TAღRIN ZღCIYA 💖🌺💍 ( RETღRN ) ( ROMANTIC LUV STORY )💋🔥 ❤👑 ꪑꪖꪶꪶꪖƙỉ᭢ ꪖꪑꫀꫀꪹꪖꫝ ꪖꪉᦔꪮꪗꪶꪖꪗꫀ 👑❤ 𝗔.𝗞.𝗔 𝐀𝐍𝐈𝐒𝐇❥ 🕊💞 Marubuciyar littafin TAURIN ZUCIYA EXILED PRINCE ( LOVE MEETS POWER ) TWO LIGHTS ( YAR JARIDA ) and now TAURIN ZUCIYA ( RETURN ) Dedicated to me first 😎💜👌 and all of Army 💜🕊 Wannan littafin sadaukawar ne ga Fatimah Zarah Musa , Khadija Sabi'u ( Nainarh Nkd's ) , ga sister di ta Walee 😄😄 , da wa kuma 🤔🤔🤔🤔 ? ? ? ? , tom su na dayawa gaskiya 😂😂 Amma zan so ku sani ina godiya sosai da irin gudun mawar da na ke samu da ga gare ku , comment , sharing , duk ina godiya , Allah ya saka 🙏🙏 GARGADI !!!!!!!!!!!!!!! * ban yarda ba wani ko wata ta sauya min ko guntu a cikin abin da na rubuta ko ayi audio da shi , i dan kuma na fadin wani abu ba daidai ba a cikin littafin ku yafe mun , duk wanda ya zage ni kuma ko yayi mun mumuna fahimta to cen ta matse mishi ni ba ruwa na 😎😎 * FOR MORE INFORMATION KU TABO WANNAN NUMBER +22798999753 WHATSAPP ONLY , Thanks 👍💕 اللَّهُمَّ صَلِّ عَلَى مُحَمَّدٍ وَعَلَى آلِ مُحَمَّدٍ، كَمَا صَلَّيْتَ عَلَى إِبْرَاهِيمَ وَعَلَى آلِ إِبْرَاهِيمَ، إِنَّكَ حَمِيدٌ مَجِيدٌ، اللَّهُمَّ بَارِكْ عَلَى مُحَمَّدٍ وَعَلَى آلِ مُحَمَّدٍ، كَمَا بَارَكْتَ عَلَى إِبْرَاهِيمَ وَعَلَى آلِ إِبْرَاهِيمَ، إِنَّكَ حَمِيدٌ مَجِيدٌ️ BY : 𝔸𝑵Ɩ𝘚Η 👑❤ ( 🄼🄴🄴🅁🄰🄷 ...... ❦) Wattpad : @bennybite DOMIN SAMUN BOOK DI NA DA GA FARKO ZA KU IYA ADDING CHANEL DI NA TA WANNAN LINK 👇👇👇👇👇👇 https://whatsapp.com/channel/0029VaGhJCqKmCPUvpvIJ80i TAP THIS LINK TO JOIN MY WHATSAPP GROUP COMMETS SECTION 👇👇👇👇👇👇 https://chat.whatsapp.com/LWmuu0yv6C9DAhpdepDb4i 𝗧𝗔𝗣 𝗧𝗛𝗜𝗦 𝗟𝗜𝗞𝗘 𝗧𝗢 𝗝𝗢𝗜𝗡 𝗠𝗬 𝗣𝗢𝗦𝗧𝗜𝗡𝗚 𝗥𝗢𝗢𝗠 👇👇👇👇👇👇👇 https://chat.whatsapp.com/LepRstkGv3sDf8Jj4Gm054 _________________✦✦✦✦✦✦✦✦✦✦✦✦✦✦✦__________________ [ 🅿🅰🅶🅴̥ 1 ❤🔥 ] BISMILLAHIRRAHMANIRRAHIM AFTER SOME YEARS 🤧 NA SAN A NAN KOWA ZAI TAMBAYE NI ME YA FARU DA WANNAN AHALIN TOM NI MA BAN SANI BA SABODA BA NA NAN BARE NA YI RAHOTO , AMMA DAI NA SAN BABY TA RASU SEVEN MONTH BAYAN RASUWAR BIBI WAJEN HAIHUWA DA ITA DA BABYN TA DUK SU KA KOMA GA ALLAH , A RANAR SAI DA RAYAN YA YI ZAUNE YA NA KUKA KAMAR KARAMIN YARO , KO ONE MONTH BA A YI BA DA MUTUWAR TA YA TAFI WATA MISSION HAR YA SHARE WAJEN GOOD EIGHT YEARS BABU SHI BA MAI KAMA DA SHI , NIHAL KUWA TA CI GABA DA KULA DA JUNIOR A CIKIN SHEKARUN NAN TAKWAS DA RAYAN BA YA NAN ABUBUWA DAYAWA SUN FARU A CIKI HAR DA RASUWAR DADDY , ANIR KUMA YA TATTARA FAMILYN SHI YA KOMA UK DA SU , ANAS KUMA SU KA KOMA DUBAÏ TARE DA UMMA SU KA BAR NIHAL DA AYLAN KADAI A US BAYAN SHEKARA BIYAR DA KOMAWAR SU DUBAÏ ITA MA UMMA TA RASU IDAN MU KA LEKO YARAN KUWA BAYAN LITTLE YA CIKA SHEKARA TAKWAS AYLAN YA FARA BA SHI HORON SOJA , BA ROKON DA NIHAL BA TA MISHI BA A KAN YA BARI YA KAI SHEKARA 15 AMMA FIR YA KI YARDA , BA YADDA ZA TA YI SAI SA MUSU IDO , TA NA JI TA NA GANI YA MEDA KARAMIN YARO KWARAREN SOJA , DA GA HARBIN BINDIGA HADA BOMBS , FADA DA MAKAMI HAR DA HANNU DUK SAI DA LITTLE YA KOYE SU KAFIN MA YA CIKA SHEKARA GOMA BAYAN YA CIKA SHEKARA GOMA SHA BIYAR YA DAUKE SHI TARE DA JUNIOR YA KAI SU MILITARY CAMP SU KA FARA KARBAR HORON SOJA A TARE SU NA A HAKA HAR RAYAN YA DAWO DA GA MISSION DIN SHI , DA FARKO YA SO YA YI JA A KAN HUKUNCIN AYLAN NA KAI SU MILITARY CAMP HAR MA YA JE DAWO DA SU AYLAN BAI SANI BA , AMMA FIR LITTLE DA JUNIOR SU KA KI YARDA SU KOMA A BAR ZANCEN LITTLE FUSKAR MAGANAR MA BAI BAYAR BA DAN YANZU MISKILANCIN YA FI NA FARKO GA WATA ZUCIYA DA YA DAUKO , KO AYLAN YA KAWO MISHI ZIYARA BA YA KULA SHI KAMAR BA MAHAIFIN SHI BA NIHAL DAI TA NA GEFE TA NA KALLO BA TA DA IKON YIN MAGANA , TA NA CEN TA NA FAMA DA IQBAL GA KUMA SABON BABY DA SU KA SAMO WANDA YA CI SUNAN VEDAD YA NA KAMA DA AYLAN SAI DAI KANANAN IDANUN GARE SHI SKY BLUE EYES IRIN NA MAHAIFIN SHI GA KUMA JARABAR UMMI GEFE DAN AYLAN YA BI YA SANGARTA TA KO YARINYAR PRESIDENT BA TA GWADAWA UMMI SANGARTUWA DAN DUK CIKIN YARAN SHI YA FI SON UMMI SAI VEDAD BAYAN SHEKARUN UKU AYLAN YA NEMI TAKARAR SHUGABAN KASSAR US KUMA CIKIN SA'A YA LASHE PRIMARY ELECTIONS TWO WEEKS BAYAN PRIMARY ELECTIONS , A KA DASA BOMB A CIKIN MOTAR SHI YA FITO DA GA HEADQUATER DIN SU MOTAR TA TASHI DA SHI A CIKI KO KASHIN SHI BA A SAMO BA KUMA HAR ZAMAN YANZU BA A SAMO WANDA YA YI WANNAN AIKIN BA NIHAL HAR DOGUWAR SUMA TA SHIGA , SAI DA TA SHARE ONE YEAR CIKIN DOGUWAR SUMAR TA BA TA FARFADO BA DUK WANI BINCIKE DA RAYAN ZAI YI SAI DA YA YI SHI AMMA BAI GANO WANDA YA YI HAKAN BA , BA YADDA YA IYA HAKA YA RUNGUMI SORRY YA CI GABA DA KULA DA YAR UWAR SHI , DA KUMA YARAN BIG BRO DIN SHI SPECIALLY VEDAD DAN A LOKACIN BA ZAI WUCE SHEKARA BIYAR YA YI DUK WANI KOKARI DA ZAI YI DAN GANIN BAI JI KADAICIN MAHAIFIN SHI BA DUK ABUN NAN DA YA FARU LITTLE DA JUNIOR SU NA CEN A MILITARY CAMP BA SU FITO BA KO AN BA SU DAMAR TAFIYA GIDA SAI DAI JUNIOR YA TAFI SHI LITTLE BA YA TAFIYA A HAKA HAR SU KA CIKA SHEKARA 25 BAYAN YA KAMALA TRAINING DIN SHI SU NA FITOWA KO RAYAN YA ZAMA PRESIDENT OF UNITED STATES BABU WANDA BAI YI MAMAKIN HAWAN SHI KUJERAR PRESIDENT LOKACI GUDA HAKA DAMA CIKIN DUHU YA YI AIKIN SHI GUDUN KAR A MISHI IRIN NA AYLAN A HAKA YA MEDA LITTLE MILITARY CAMP INDA ZAI FARA KARBAR SABON TRAINING NA ZAMA THE GENERAL OF AMERICAN ARMY STAFF , JUNIOR KUMA HIS MARSHAL BAYAN SHEKARA UKU YA FITO A MATSAYIN GENERAL OF AMERICAN ARMY STAFF A SHEKARA 28 IDAN AYLAN YA YI TAURIN ZUCIYA LITTLE YA CE MISHI BA KA SAN KOMAI BA , DAN RAYAN SAI DA YA FARA NADAMAR MEDA SHI MILITARY CAMP DA YA YI HMMMM NI DAI ABUN DA NA SANI KENNAN YANZU BARI MU SHIGA LABARIN MU ▪UNITED STATE ( WASHINGTON DISTRICT DE COLUMBIA ) wani makeken gidan ne , wannan ya yi kadan a ce mishi makeke dan unguwa guda ce wannan gidan kofar shi ma kadai abun kallo ce Tu da ga farkon layin gidan wasu jibga jibgan sojoji ko wane rike da manyan bindigu , su na tsatsaye kamar an dassa su a wajen fuskokin su a daure tamau kamar hadari Da ga cikin gidan kuma harabar gidan ma kadai ta isa a gena madaidaicin gidan har ashirin dan ba karamin fili ba ne ni gaza ganin karshen shi ma na yi harabar gidan Cike ta ke sojoji kowane rike da gun sai kai kawo su ke A geffen dama wani makeken parking space cike da motoci 50 ma albarka dan na kassa kirga su , da ga gani kuma ba kananan motoci ba ne dan guda dai ma sai ta sayi gida sukutum , ko wace colour akwai har golden , grey , pink Dan nesa kadan da parking space din wani Filin wassan ball ne mai mugun girma , geffen shi wata yar Runfa ce shake da chair kamar dai irin na Stadium , a bayan su kuma akwai wani closet dauke da ball kala kala , na football , basketball , handball , baseball da bat din su , gloves irin na box da wasu sanduna bakake Ka na fitowa parking space wata doguwar hanya ce zagaye da ciyayi da flowers mai mugun kyau Daguwar hanya ce , a kila ka yi tafiyar minti biyar kafin ka iso wani tanpasheshen building mai hawa uku Fari kal da shi , a hawa na ukun akwai wani katon balcony , idan ba ka hau ba ba ka iya ganin abunda ke cikin balconyn , duk wasu Windows na wajen na glass ne Wata kofar ta glass na nufa wadda za ta sada ka da parlourn gidan Ka na isowa bakin kofar wata wuta blue ta ke fitowa ta yi scanning da ga sama har kassa kafin kofar ta bude slowly da kan ta Wani irin sanyi ne mai mugun dadi da kamshi zai fara kai ma ka karo kafin ka shiga cikin gidan ma A hankali na daga kafa na shiga wajen nan na ga abun da ya fi karfin alkalami na , dan ya yi kadan ya fada muku abun da na gani , wannan wajen sai dai a kira shi da aljannar duniya baki daya ma Komai na cikin wajen da ga sky blue da navy blue sai white colour abun ba karamin kyau ya kara mishi ba ( Ni dai ba zan iya fada muku abun da na gani ba gaskia 😴 ku bari idan mu ka tsunduma cikin labarin za ku ga yanayin gidan yawwa 😌🤙) A hankali wata kyakyawar budurwa ta ke sauko wani stair mai mugun kyau zagaye da glass ba dan kar ku ce na yi karya ba da sai na ce stair din da kan shi na glass Kyakyawa ce ajin farko fara kal da ita kamar ka taba jini ya fito da ga gani kassan renon madara da ice cream ne , ta na kama rai da rai da Aylan kamar an tsaga kara sai dai idanun ta tak irin na Nihal ne Ta na sanye da mini skert dai'dai guyiwa pink colour , da wata t-shirt White colour da kadan ta wuce cibi ta daura wata jacket pink colour ita ma , ta saka wasu sneakers farare kal kamar ba kassa a ke takawa da su , ta na rataye da wata yar bag a shoulder hannu ta rike da wata dankareriar waya golden colour har wani shining ta ke , dayan hannun kuma ta na rike da wata coat Fara Sai da ta gama sauko stair din ta na tafiyar kamar da ga saman ta jiyo Muryar wata mata ta na fadin " ke ke , ummi ina za ki je da wadanan kayan haka ? " ta fada da turanci Cak budurwar nan ta tsaya ta daga kai sama ta na lumshe idanun ta a hankali kafin ta sake bude su slowly ta juya ta na kallon matar da ke tsaye a bayan ta Ba kowa ba ce face Nihal , ta na sanye da wata Abaya sky blue colour mai mugun kyau ta yi Rowling veil din ta , ta na nan yadda ta ke ba abun da ya sauya na ta , sai dan shekaru da su ka ja dan gaskia yanzu an dan lattijantaka amma duk da haka ta na nan kamar yar shekara 20 don gaskia jikin ta ya na samun kula , har wani haske skin din ta ya kara ta zama kamar baturiya " mummy , me kaya na su ka yi kuma da za ki tseda ni , zan yi late a wajen aiki " ummi ta fada ta na marairaice fuska Tsuke fuska Nihal ta yi ta na nuna ta da yatsa ta ce " ke Ummi wlh ki kiyaye ni , maza koma ki canza min kayan nan " Dan bubuga kafafun ta kassa ta yi cikin shagwaba ta ce " haba mummy ni fa ba yarinya ba ce da za ki ce sai kayan da ki ke so zan saka , shekara daye daye daye har 29 gare ni ina cikin ta 30 amma kullum kamar baby ki ke dauka ta , ya ishe ni haka " Takowa Nihal ta yi ta tsaya dab da ita ta ce " Ummi ke fa ba yarinya ba ce yanzu har shekara 29 ba ki da saurayi tsayaye bare a yi zancen aure , na lura da ke da yan uwan ki duk ba ku son zancen , wai sai kun tsufa kun zama kamar ni za ku yi auren ne , kin san dai da wannan shekarun na ki da wuya ki samu mijin aure a nan kusa ba , ko yaron uncle Junaid da ya zo ganin ki sai da ki ka sakin mishi karnuka ya bar gidan ba shiri " Da sauri Ummi ta katse ta da cewa " Mummy , Mummy , ya isa please ni na ce miki ina da bukatar mijin aure ne , I don't need man over me , it's never my priority , dan haka ki bar min zancen wani aure , amma kin san wani abu , duk ranar da Big bro ya yi aure , ni ma a yi nawa a ranar ai dama tare mu ka shigo duniya " ta kai karshen ta na yar dariya ta juya za ta bar wajen Da sauri Nihal ta ce mata " ki dawo ki sauya kayan nan na ce miki " ta kai karshen da dan karfi Ba tare da ta juyo ba ta daga mata hannu ta na fadin " sai na dawo Mummy , I love you " ta kai karshen ta na ficewa falon Da kallo Nihal ta rakata har sai da ta bar wajen sannan ta yi dan karamin murmushi ta na girgiza kai ta juya ta koma inda ta fito * MISALIN KARFE 9 NA YAMMA Zaune mutanan gidan su ke cikin wani makeken dining room , dauke da wata dining table mai bala'in kyau fara kal mai kujeru 10 duk kujerun kuma farare ne Table din shage ta ke da kayan cima , da ga snacks , fruits , juice , water , abinci kala kala Cen na hango Ummi zaune saman chair din ta ta na faman latsa waya , ga wasu samari guda hudu , sai wani babban mutun da ke zaune ya na kallon su , kallon daya na yi mishi na gane Rayan ne Duk da yanzu shekaru sun ja , ya dan lattijantaka , ga kuma kyasumba da ya tara amma har yanzu ya na nan yadda ya ke , har wannan murdaden jikin nashi Cen kuma na hango wani kyakyawan sauri ya na zaune geffen daman Rayan Kamanin shi sak Aylan , kamar an tsaga kara har wadanan sexy blue eyes sak iri daya , da wannan darck black curly hair din na shi kai har wannan murdaden jikin , ni da farko na zata Aylan din ne , tabass little ne wannan A hankali ya dago kan shi ya kali Ummi da su ke fuskantar juna ya ce mata " Ummi je ki kira mummy har yanzu ba ta fito ba " ya fada kamar an yi mishi dole Ko dago kai ba ta yi ba ta kale shi bare ta yi abun da ya ce mata Shi dai ya tsare ta da wadanan sexy blue eyes din na shi babu ko kiftawa Ya na shirin magana Rayan ya mike da saman chair din shi ya na fadin " ku bari jan je na kira ta " ya kai hannu ya na fara takawa ya fice dining room din Ya na barin wajen wani saurayi da ke zaune geffen little ya ce " mutun sai son girma kamar dollar , wannan girman ka bar shi a headquater , a nan akwai wanda su ka girme ma ka " Slowly little ya mike tsaye ya mika ma Ummi hannu ya ce " please come with me " Ba musu ta mike tsaye sannan ta zagayo ta geffen shi ta daura hannun ta saman na shi su ka bar dining room din a tare Ya rage su uku , junior da wasu samari biyu da su ka sunkuyar da kan su ban iya ganin face din su gaskia Kai tsaye dakin da Nihal ta shiga da safe su ka nufa Su na shigo part din ko , Rayan ya shiga bedroom din Su na shigowa ya kali Ummi ya ce " yi shiru ki saurara " ya kai karshen ya na sakin hannun ta , su ka karaso bakin kofar bedroom din su ka yi tsaye Bangaran Rayan kuma ya na shigowa bedroom din ya na sallama kassa kassa Nan ya ga Nihal zaune bakin gado ta na rike da wata laptop ta na faman hawaye bibiyu kamar an bude fanfo Slowly Rayan ya karaso ya zauna geffen ta ya sa hannu ya amshe laptop din ya ajiye geffen shi ya sa hannu ya talabo face din ta ya na fadin " Sister , wai sai yaushe wannan abun ne zai kare ? Ba ki gajiya kullum ki shigo daki ki yi ta kuka ke kadai " A hankali wani siririn kuka ya kubce mata ta na fadin " yaya Rayan ba zan iya ba , na kassa wlh , why zai tafi ya bar ni , why mutuwa za ta min haka me na yi mata , ji na ke kamar na kashe kai na , na huta , rayuwa babu shi sam ba rayu ba ce a waje na , yanzu ya tafi ya bar ni har abada kenan " A hankali Rayan ya kai hannun shi ya janyo ta jikin shi ya rungume ta ya na fadin " ya isa haka sister please , ki daina cutar da zuciyar ki , yanzu inda ya san halin da ki ke ciki ya ki ke tunanin zai ji , in su Ummi su ka gan ki cikin wannan halin me za ki ce musu " Da sauri ta katse shi da cewa " su ma cikin wannan halin su ke , na san su na kewar Daddyn su sosai , amma na kassa maya gurbin shi a rayuwar su , na kassa rike amanar da ya bar min , ya ka ke tunani in ya San halin da Ummi ta ke ciki , ka fi kowa sanin ita ce sanyin idaniyar shi , ko cikin yaran mu ya fi son ta fiye da kowa ne , amma yanzu duba irin halin da ta dauko , Sallat ma sai na dinga sa ta a gaba ta na yi , na san ko da ya na raye , idan ya ga yadda ummin shi ta zama na san sai zuciyar shi ta buga , duk laifi na ne , na kassa ba su tarbiyar da ta dace , ya bar min abin da ya fi mishi komai daraja a rayuwar shi amma ni na watsar da ita , yaya Rayan ji na ke kamar na mutu ni ma na tarda shi in da ya ke " A hankali little ya turo kofar dakin ya shigo ya na fadin " mummy ke ma tafiya ki ke son yi ki bar mu ? " Da sauri Nihal ta boye fuskar ta a kirjin Rayan ta na kara sautin kukan ta Ci gaba da takowa ya yi ya zo gaban ta ya tsuguna ya riko hannayanta ya ce " mummy please stop crying , ba na son ganin ki cikin wannan halin , so ki ke ki karaya mana zuciya , Daddy ya tafi ya bar mu , kema ki tafi ki bar mu ? Ya ki ke so mu yi ? Please mummy ki daina kar ki janyo wa kan ki wata illa " Slowly Nihal ta fara rage sautin kukan ta , ta shiga sauke ajiyar zuciya Ya na jin hakan ya mike da ga tsugunin da ya yi ya koma saman bedside drawer ya zauna ya na kallon mummyn ta shi Bai fi two minutes da zama ba Ummi ta shigo dakin kai a sunkuye ta na tafiya kamar wadda a ka daure kafafun ta Gaban Nihal ta karaso ta Zube saman guyiwowin ta , ba tare da ta dago kai ba ta ce " i'm sorry mummy , na san na dauki tsawan shekaru ina bata miki rai , please forgive me , na san inda Daddy ya na nan ba zai taba yin alfahari da ni ba , duk tarbiyar da ya ba ni kafin ya tafi na yi watsi da ita na dauko wadda ba tawa ba , mummy ina kewar Daddy na sosai , har yanzu ban gama grief din shi ba , ko wace safya idan na tashi na shigo bedroom din ki na ga ke daya ce duk sai na fara danasanin zowa da yi , shi ya sa ki ka ga na daina zuwa gaishe ki da safe , mummy kar ki ce za ki tafi ki bar ni wlh ba zan iya jure rashin ku ba cikin rayuwa ta , duk irin rashin kunyar da na ke yi miki ba dan ba na son ki ba ne wlh mummy ina son ki fiye komai a rayuwar nan idan ke ma ki ka tafi ki ka bar ni wlh ni ma sai na bi ki , ke kadai ce na ke iya kallo na rage radadin rashin Daddy kusa da ni " kassa ci gaba da maganar ta ta yi sakamakon kukan da ya ci karfin ta A hankali Nihal ta dago kan ta , ta talabo fuskar Ummi ta ce " Ummi na ya isa haka ki daina kukan nan kin ji ko ? " ta fada mata cikin sanyi Mikewa tsaye Ummi ta yi ta dawo geffen Nihal ta zauna sannan ta rungume ta ta na fadin " i love you my mummy " Dan karamin murmushi Nihal ta yi ta na fadin " ni ma ina son ki Ummi na " Murmushi mai dan sauti Rayan ya yi kafin ya kali Little ya ce mishi " Little ! Je ka kawo mana abinci a nan za mu yi dinner " Tsuke fuska ya yi ya na kallon Rayan ba tare da ya ce komai Yar karamar dariya Rayan ya yi kafin ya ce " sorry General Ash , je ka kawo mana abinci " Bai gama rufe bakin shi ba wani saurayi ya shigo dakin ya na rike da wani tray ya ce " ba sai ya je ba mun kawo " Saurayin ya na kama sak da Nihal kamar an tsaga kara har colour din idanun brown a shekaru zai kai 24 years haka Cikin dakin ya karaso ya tsaya gaban Nihal ya ajiye tray din kassa saman dan carpet da ke bakin gadon sannan shi ma ya zauna sama " to malam sai ka je ka kira Vedad " Ash ya fada ya na kallon shi ( kar ku ce ba ku gane ba Ash ba kowa ba ne face Alyasat 😴😴 da haka su ke kiran shi yanzu , ni ma ban san dalili ba ) Noke kafada ya yi ya na shirin magana dayan saurayin ya shigo ya na rike da tray din fruits Shi kuma wannan ya so ya dan yi kama da Aylan , sai dai shi ya na da kananan idanu farare kal amma kwayar cikin su Sky blue da ita har wani kyali ta ke gwanin burgewa a shekaru ba zai wuce 20 years ba Geffen saurayin nan shi ma ya zauna ya ajiye tray din gaban shi Shagwabe fuska ya yi ya na kallon Nihal ya ce " mummy , sauko ki ci , ko na cinye abu na dan ni fa gaskia yunwa na ke ji " Saurayin da ke geffen shi ya dunkule hannun ya kai mishi bugu a damtse ya na fadin " Wai kai Vedad yaushe za ka daina wannan shirmen , ba fa yaro ne kai ba " Vedad na shirin magana Nihal ta riga shi cewa " Iqbal , wlh ka daina buga min auta na " ta fada cikin tsare gida Ummi da ke zaune geffen ta ta ce " mummy wlh duk ke ki ka goyawa Vedad baya ya na yi mana abun da ya ga dama , da an taba shi ki ce uban wa " Yar karamar dariya Nihal ta yi kafin ta sauko kassa ita saman carpet din Ta na zama Vedad ya yi sauri ya koma gefen ta ya zauna ya na murmushi Ita ma Ummi saukowa ta yi ta koma dayan geffen Nihal ta dauki plate ta ajiye ma kowa gaban shi ta fara serving din su Ta na farawa Rayan ya mike tsaye a hankali ya nufi kofar fita dakin ya ficewar shi ya bar ta tare da yaran ta ya na fita Ash ya mike shi ma ya bi bayan shi Da sauri Nihal ta ce mishi " Ash ! Ba za ka ci tare da mu ba ne " Ba tare da ya tsaya da ga tafiyar shi ba ya ce " ina zuwa mummy " ya kai karshen ya na ficewar shi Rayan na shirin barin part din Ash ya ce mishi " His excellency ina son mu yi wata magana " Cak Rayan ya tsaya ya juyo ya na kallon Ash da ya ke tunkaro shi fuska dauke da murmushi Shi kuma Ash ya na karasowa gaban Rayan ya dai'dai ta tsayuwar shi ya rike hannayan shi a baya ya ce " His excellency..... " Da sauri Rayan ya katse shi da cewa " Ash wai ba za ka daina kira na da his excellency ba , yanzu fa a gida mu ke " Sakin hannayan shi Ash ya yi ya ce " okay uncle, ina so zan je Nigeria wajen wani aiki, so ina son ka kira Mr president ka fada mishi ya shirya mana gidan da za mu sauka " " no ba sai an yi haka ba , mu na da gida je a Nigeria kawai in ka tashi tafiya ka fada min , kai da wa za ka tafi ne ? " Sai da ya dan dauki lokaci kafin ya ce " all " a takaice Cike da rudu Rayan ya ce " ban gane ba " " uncle , aiki ne zan tafi yi a cen so ina da bukatar Junior tare da ni , na fadawa mummy ta ce ita ma za ta je domin yin wani aiki , shi ya sa na ce su shirya mu tafi baki daya " Shiru Rayan ya yi ya na kallon shi na dan lokaci kafin ya ce " dan ka San ba zan iya biyar ku ba ne za ka min haka , yanzu ya zan yi cikin gidan nan ni kadai ? " " zan so ka koma White house kafin mu dawo " " okay yanzu yaushe za ku tafi " " next week " " okay , Allah ya ba da sa'a " ya na gama fadar haka ya juya ya ficewar shi Da amine Ash ya amsa mishi cikin zuciyar shi kafin shi ma ya juya ya koma cikin bedroom din Nihal ya na sallama kassa kassa Yanayin da ya tardo su abun ba karamin sanyaya mishi zuciya ya yi ba , kawai sai ya koma saman bedside drawer ya zauna ya na ci gaba da kallon su , su na cin abincin su su na dariya , Vedad kuma Nihal na ba shi a baki kamar karamin yaro Bangaran Rayan kuma kai tsaye dining room ya koma Nan ya tardo junior zaune shi kadai ya na faman latsa wayar shi TAღRIN ZღCIYA 💖🌺💍 ( RETღRN ) (ROMANTIC LUV STORY )💋🔥 ❤👑 ꪑꪖꪶꪶꪖƙỉ᭢ ꪖꪑꫀꫀꪹꪖꫝ ꪖꪉᦔꪮꪗꪶꪖꪗꫀ 👑❤ 𝗔.𝗞.𝗔 𝐀𝐍𝐈𝐒𝐇❥ 🕊💞 Wattpad : @bennybite Marubuciyar littafin TAURIN ZUCIYA EXILED PRINCE ( LOVE MEETS POWER ) TWO LIGHTS ( YAR JARIDA ) and now TAURIN ZUCIYA ( RETURN ) FOR MORE INFORMATION KU TABO WANNAN NUMBER +22798999753 WHATSAPP ONLY , Thanks 👍💕 اللَّهُمَّ صَلِّ عَلَى مُحَمَّدٍ وَعَلَى آلِ مُحَمَّدٍ، كَمَا صَلَّيْتَ عَلَى إِبْرَاهِيمَ وَعَلَى آلِ إِبْرَاهِيمَ، إِنَّكَ حَمِيدٌ مَجِيدٌ، اللَّهُمَّ بَارِكْ عَلَى مُحَمَّدٍ وَعَلَى آلِ مُحَمَّدٍ، كَمَا بَارَكْتَ عَلَى إِبْرَاهِيمَ وَعَلَى آلِ إِبْرَاهِيمَ، إِنَّكَ حَمِيدٌ مَجِيدٌ️ DOMIN SAMUN BOOK DI NA DA GA FARKO ZA KU IYA ADDING CHANEL DI NA TA WANNAN LINK 👇👇👇👇👇👇 https://whatsapp.com/channel/0029VaGhJCqKmCPUvpvIJ80i TAP THIS LINK TO JOIN MY WHATSAPP GROUP COMMETS SECTION 👇👇👇👇👇👇 https://chat.whatsapp.com/LWmuu0yv6C9DAhpdepDb4i 𝗧𝗔𝗣 𝗧𝗛𝗜𝗦 𝗟𝗜𝗞𝗘 𝗧𝗢 𝗝𝗢𝗜𝗡 𝗠𝗬 𝗣𝗢𝗦𝗧𝗜𝗡𝗚 𝗥𝗢𝗢𝗠 👇👇👇👇👇👇👇 https://chat.whatsapp.com/LepRstkGv3sDf8Jj4Gm054 _________________✦✦✦✦✦✦✦✦✦✦✦✦✦✦✦__________________ [ 🅿🅰🅶🅴̥ 2 ❤🔥 ] BISMILLAHIRRAHMANIRRAHIM Saman chair din shi ya koma ya zauna ya na shirin magana junior ya riga shi cewa " ashe ba ka manta da ni ba " " why zan manta da kai ? " Rayan ya fada ya na serving din kan shi Ajiye wayar shi gefe junior ya yi sannan ya fara serving din kan shi, shi ma sannan ya ce " ka saba yi min hakan ai " Dakatar da abun da ya ke yi Rayan ya yi ya kali junior ya ce " Aylan junior ........ " Da sauri junior ya katse shi da cewa " please Dad why ba za ka iya kira na da Aylan kai tsaye ba kullum sai ka kara da junior , ko sunan ne bai dace da ni ba " Dan karamin murmushi Rayan ya yi kafin ya ce " Junior , ba za ka gane ba ne , ina jin yaunin kiran sunan nan kai tsaye , me ya sa ba ka iya fahimta ta ne ? " Daukar spoon junior ya yi ya fara cin abincin shi kafin ya dauki wayar shi ya ci gaba da latsawa " junior ! " Rayan ya fada a sanyaye Ko kallon shi junior bai yi ba , sai ma ci gaba da cin abincin shi da ya yi Shiru Rayan ya yi ya na ci gaba da junior Sai da ya dauki wajen good three minutes a haka kafin Rayan ya ce " junior , na san abun da ke damun ka , ni ma......... " Da sauri junior ya katse shi da cewa " stop Dad please , ka daina cewa ka san abun da ke damu , ba abun da ka sani a kai na , idan na tambaye ka what is my favorite colour , na san ba za ka iya ba ni amsa ba , tun bayan Rasuwar Momy duk ka daina kula ni " " junior ! Ka fi kowa sanin irin son da na ke yi maka you are my only son " " where is this love Dad ? Kullum sai ka ce ka na so na amma duk son nan da ka ke cewa , cousins din na ka ke nuna wa , duk soyayyar da ya kamata a ce ni na same ta da ga gare ka su ka ke nuna wa " junior ya fada da dan karfi Riko hannun shi Rayan ya yi ya na fadin " please my junior calm down....... " Kwace hannun shi junior ya yi ya na fadin " Stop that , it's late now , tun baya ya kamata a ce ka gyara amma sai ka yi watsi da abun " " Junior , don't forget i'm your Dad , duk duniyar nan babu wanda zai cewa ya fi ni son ka , na san har yanzu ka na radadin mutuwar momynka , ni ma ina radadin mutuwar matata , kai kadai ne ka rage min da ga ita , don't say you hate me please wlh ba zan iya jurewa ba " Rayan ya fada idanun shi na kawo ruwa Kallon wutsiyar ido junior ya yi mishi kafin ya mike tsaye ya dauki wayar shi ya fice dining room din " Junior, where are you going ? " Rayan ya fada shi ma ya na mikewa tsaye Bai amsa mishi tambayar shi ba , ya nufi stair ya Haye da sauri ya bar Rayan shi kadai a dining room Komawa Rayan ya yi ya zauna Kamar da ga sama ya jiyo Muryar Ash ya na fadin " yaran yanzu sai a hankali ko his excellency ? " Da sauri Rayan ya dago kan shi , ya na tsaye gaban shi ya saka hannayan shi a aljihu Murmushin karfin hali Rayan ya yi kafin ya ce " Ash , junior fa ya girme ka , shi ne za ka ce mishi yaro " A hankali Ash ya fara takowa ya karaso cikin dining room din ya ja chair din da ke geffen Rayan ya zauna , ya jingina bayan shi a jikin chair din ba tare da ya ciro hannayan shi da ga cikin Aljihun shi ba ya ce " uncle ni da Junior sati biyu ne kawai ke tsakanin mu , duka 29 years gare mu , so ka daina cewa ya girme ni , na ga shi ma cewa ya ke ya girme ni " Hararrar shi Rayan ya yi kafin ya ce " to kariya ya yi ne ? Ko ba komai ya riga ka shigowa duniya " Kauda kan shi gefe Ash ya yi ba tare da ya ce komai ba Yar karamar dariya Rayan ya yi kafin ya ce " to Shikenan , General ya Batun auren ku kuma , kun ga Mimi da Ayna sun yi auren su har da babys din su me kuke jira kai da junior da Ummi ko so ku ke sai kun tsufa sannan " Slowly Ash ya dawo da kallon shi kan Rayan " aure sai dai Ummi da junior su yi , amma ni dai babu gurbin mace a cikin rayuwa ta " Dariya sosai Rayan ya yi har sai da wasu hawaye su ka zubo mishi Sai da ya Kamala dariyar shi sannan ya ce mishi " kar ka damu , haka shi ma Dad din ka ya ke fada , amma dubi yadda soyayya ta kama shi , har mutuwa zai iya yi a kan sister , saboda ita ya daina zuwa headquater sai dai ya bar min aiki shi ya dawo ya zauna tare da ita , ko Daddy da ya haifeshi bai taba ganin murmushin daddyn ku ba sai sister , saboda irin son da ya ke mata har zubewa ya yi saman guyiwowin shi ya na ba ta hakuri kamar yadda a ke rarrashin baby , yanzu a tunanin ka inda wani a baya ne wani ya fada mishi zai yi duk wannan abun ka na ganin zai yarda " " Uncle , Daddy ka ce ba ni ba , babu macen da ta isa na zube saman guyiwowi na gaban ta , wai da sunnan hakuri , uncle har yanzu ba a yi ta ba " ya kai karshen ya mike wa tsaye ya fara takawa ya fice dining room din Da kallo Rayan ya raka shi har sai da ya fice dining room din sannan ya bushe da dariya ya na fadin " za ka shigo hannu kai ma " da ga haka ya ci gaba da cin abincin shi har ya ma manta da maganar da su ka yi shi da junior Bangaran Ash kuma kai tsaye stair ya Haye , wajen kamar dan balcony ne , an saka mishi wasu sofas farare kal kamar parlourn Part bakwai ne a saman , na farko shi ne na Rayan , na biyu kuma na Ummi , sannan na Iqbal , sai na Vedad , da na Junior shi kuma Ash na shi ya na karshe kuma duk cikin part din na shi ya fi girma Kai tsaye part din shi ya nufa , har ya wuce part din junior ya tsaya cak Slowly ya juyo ya nufi door din , ya daura yatsar shi saman finger print , saboda duk kofofin da finger print su ke buduwa Ya na daura wa kofar ta yi wata yar karamar kara sannan ta bude kan ta A hankali ya shiga part din , parlourn ya na da dan girman , komai na cikin shi navy blue ne wajen ya tsaru gaskia Ya na shigowa parlourn ya ga junior zaune saman doguwar sofa ya na rike da maltina a hannu daya hannun kuma ya na rike da taba Karasowa cikin dakin Ash ya yi sannan ya zauna saman sofa geffen Junior ya zuba mishi wadanan sexy blue eyes din shi ba tare da ya ce komai ba Juyowa Junior ya yi ya kali Ash ya ce " what are you doing here ?" Shiru Ash ya yi bai ce mishi komai ba sai da ya dauki wajen good ten minutes kafin ya ce " what are you doing ?" Dan murmushi Junior ya yi ya kai tabar shi a baki ya busa kafin ya ce " smoking " ya kai karshen ya na kai maltinar shi a baki ya sha kadan Slowly Ash ya kai hannu ya karbi Tabar hannun junior ya daura saman table Cike da nitsuwa ya ce " junior you are a soldier , na zata ka daina bushe bushen ga " Dan karamin tsaki junior ya yi ya na kai maltinar shi a baki ya sha ya na kauda kai gefe " please Ash let me , wlh ba na jin dadin zuciya ta ne , shi kadai ya ke rage min radadin da na ke ji " Mikewa tsaye Ash ya yi ya na fadin " Junior , na san tun da mu ka taso ba wani sake maka fuska na ke yi ba , but don't forget ni dan uwan ka ne , duk wani abu da ke damun ka za ka iya fadamin , ba ka tsaya ka na cutar da kan ka ba " ya na gama fadar haka ya juya ya fara takawa cike da nitsuwa ya fice part din Da kallo Junior ya raka shi har sai da ya fice sannan ya sa hannu ya ciro wata yar remote da ga cikin aljihun shi ya danna wani button , nan take door din ta koma ta rufe kan ta Bangaran Ash kuma ya na fita ya koma kai tsaye part din shi , kai tsaye bedroom din shi ya wuce Bedroom din ya na da girma sosai , ga shi ta hadu kamar ba a duniya ta ke ba , komai na cikin ta white colour ne har curtain din Wata yar door ta glass ya nufa , ya na isa wajen ta bude kan ta ya shiga wani katafaren dressing room Cikin dressing room din a geffen dama akwai wata door ita ma ta glass Kai tsaye wajen door din ya nufa yanzu ma ya na tsayuwa gaban ta ta bude kan ta ya daga kafa slowly ya shiga * WASHE GARI 🌤🌤🌤🌤🌤 * NIGER ( ZINDER STATE ) * KAUYEN NAWACH KALÉ Wata kyakyawar budurwa ce ta ke tafiya a tsakiyar wata gona , ta na sanye da wani kodaden hijab navy blue har kassa Ba laifi yarinyar nan ta hadu , skin din ta Chocolate ne amma duk ya yi baki saboda dauda , ta na da dara daren idanun farare kal , kwayar cikin su kuma Ash colour ne amma bai ciza sosai ba , Idan ka gan shi da ga nesa za ka yi tunanin idanun duk farare ne babu kwaya a ciki , ta na dogayen eyelashes bakake kirin kamar ta saka mascara , eyebrow din ta su ma bakake ne a konce luff kamar ita ta zana su , ta na dogon hanci kamar pencil , da wani dan karamin bakin ta , lips din ta duk bakake ne a bushe kuma har sun dan tsatsage , a shekaru ba za ta wuce 14 years ba , amma Masha Allah ta na da shape gaskia dai'dai shekarun ta Ta na tsaka da tafiyar ta ta ji an rufe mata idanu ta bayan ta Dan karamin murmushi ta yi kafin ta bude bakin ta a hankali cikin wata yar siririyar murya ta ce " Hawa , tun dazu fa na ke jiran ji Na dauka ba za ki zo ba " Yar karamar dariya Hawa ta yi kafin ta sake mata idanu ta zagayo ta koma gaban ta ta tsaya Ta na sanye cikin wata doguwar riga green colour , da hijab zuwa guyiwa fari amma duk ya tsufa " hmmm , ki ce dai ki na son ki koma gida , dama ai saura sati biyu auren ki " Ba ta gama rufe bakin ta ba ta jiyo Muryar yarinyar nan ta saki kuka Da Sauri Hawa ta ce " Hayat ! Wlh wassa na ke yi miki , na minene kuka " Girgiza mata Hayat ta shiga yi cikin kukan na ta , ta ke fadin " a'a Hawa ba haka ba ne , wlh ba ni son auren Rabeh , ba ni son shi na tsane shi " Dafa kafadar ta Hawa ta yi cikin sigar rarrashi ta ce mata " ki yi hakuri Hayat , inda na san yadda zan yi a fassa auren nan da na yi , wlh ba na son ganin ki cikin bakin ciki , kin fi kowa sanin duk cikin kauyen nan ke daya ce aminiya ta , kowa ya san Rabeh ba mutun kirki ba ne bare matar shi Kulu , ba ta da tausayi , na san da kin shiga gidan kashe ki kawai za ta yi , Adda ya san da hakan amma ya matsa zai aura miki shi kawai dan ya fi kowa shanu cikin kauyen nan " Hannu Hayat ta sa ta fara goge hawayen ta Sai da ta gama sannan ta dago kai ta kali Hawa ta yi mata murmushin karfin hali ta ce " sai dai ki yi hakuri Hawa amma ni na yanke shawarar zan bar kauyen nan , ba zan iya auren Rabeh ba gaskia , ko matar shi ba ta kashe ni ba , na san shi sai ya kashe ni " Da sauri hawa ta katse ta da cewa " ke Hayat ki na jin abun da ki ke fada , ki bar kauyen nan ki tafi ina , kin san yadda rayuwar birni ta ke kuwa " " Hawa ya ki ke so na yi , kin fi kowa sanin duk cikin kauyen nan kallon aljana su ke yi min saboda idanun ga na wa , babu wanda ke raba ta , ko shi Rabeh dan Allah ya yi mishi mugun son mata ne kawai ya ce zai aure ni Adda kuma ya ba shi ko sadaki na bai biya ba sai ka ce wadda ba ta da gata ba dan haka ko kallo ban ishe shi ba , Adda da kan shi ya bude baki ya ce ya ba shi sadaka kawai dan ya bar gani na kusa da shi " Hayat ta fada kuka na neman kubce mata Da sauri hawa ta sa hannu ta janyo ta jikin ta ta rungume ta na dan bubuga bayan ta sigar rarrashi Sai da ta yi kukan mai isar ta sannan ta yi shiru ta na sauke ajiyar zuciya sannan ta dago a hankali da ga jikin Hawa ta na dan karamin murmushi Murmushi ita ma Hawa ta yi mata ta na kai hannayan duka biyu saman face din ta , ta goge mata hawayen ta na fadin " Shikenan yanzu ya isa haka , wuce mu koma gida , ni fa yunwa na ke ji " Yar karamar dariya Hayat ta yi kafin ta kai hannu ta dunguri kan Hawa ta na fadin " sannu sarkin ci , wuce mu tafi ni ma yunwar na ke ji " Riko Hannun ta Hawa ta yi kafin ta juya ta fara takawa ta na janye da hannun Hayat su ka bar gonar Sai da su ka dan yi nisa da tafiyar su sannan Hawa ta saki hannun ta , su na tafe su na hirar su har sai da su ka fara hango gidaje Kamar da ga sama su ka jiyo Muryar wani mutun da ga bayan su ya na fadin " ke Hayat " Cak Hayat da Hawa su ka tsaya da ga tafiyar su , nan take Hayat ta ji zuciyar ta buga da karfi har sai da ta hadiye wasu yawu Ta na haka ta sake jiyo wannan muryar ya na fadin " ba da ke na ke magana ba ? " Slowly Hayat ta juyo kai a sunkuye murya na kerma ta ce " ina kwana ? " Wani dan dattijo ne tsaye a gaban ta sam ba shi da kyan gani , a shekaru zai kai 37 haka ya na rike da wata sanda irin ta korar shanu Kare mata kallo da kyau ya yi da ga sama har kassa kafin ya kali hawa ya wurga mata wata muguwar hararra Dum ta ji gaban ta ya fadi har sai da ta dan zaro idanu , da sauri ta ce ma Hayat " Hayat ni zan tafi gida sai an jima " ta na gama fadar haka ta juya da sauri ta bar wajen Ta na barin wajen wannan mutun ya dawo da kallon shi kan Hayat ya ce " ba ni son na kara ganin ki tare da yarinyar nan kin ji na fada miki ? " A hankali ta gyada mishi kai ba tare da ta dago ta kale shi ba " shikenan wuce gida mazza kar ki tsaya ko ina " Bai gama rufe bakin shi ba ta juya da gudu ta bar wajen Shi kuma tsayawa ya yi ya raka ta da kallo har sai da ta fara kurewa ganin shi sannan ya juya ya yi tafiyar shi Ba ta daina gudun ta ba har sai da ta karaso bakin kofar wani gida na jar lakar ko kofa ba shi da wani zane ne a ka sa a ka yi mishi kariya , kun san dai yadda yanayin gidajen kauye su ke ba sai mun bata lokaci a kai ba Bakin ta dauke da sallama ta shigo cikin gidan ta na tafiya simi simi kamar barauniya Har ta karaso bakin kofar wani daki ta jiyo Muryar wata mata da ga bayan ta ta na fadin " to malama da ga ina ki ke ? " Slowly Hayat ta juyo ta kali matar ta saki wani cool murmushi ta ce " Inna na je wajen Hawa ne " Matar sam ba ta yi kama da Hayat ba , asali ma Hayat ta fi ta haske da kyau gaskia Ta na sanye cikin wasu kayan na atanfa riga daban zane daban dan kwalin ta kuma kalar zanen ta rike da kugu da hannayan ta biyu Kare wa Hayat kallo ta yi da kyau kafin ta ce " Rabeh ya zo neman ki " Da sauri Hayat ta ce " eh mun hadu saman hanya , har ya ce na gaishe ki " Dan karamin murmushi inna ta yi kafin ta sauke hannayan ta ta juya ta na fadin " je ki dauki abincin ki , tun bai yi sanyi ba " Da to Hayat ta amsa mata kafin ta nufi wani dan dakin wanda ina kyautata zaton kitchen ne Inna kuma ta nufi hararrar gidan kassan wata yar inuwa ta shanya tabarma ta zauna Dai'dai lokacin da Hayat ta fito da ga cikin kitchen din rike da wata yar kwalla ta abincin ta wani cup na ruwa ta nufi wajen da inna ke zaune ta zauna saman tabbarmar ita ma ta ajiye kwallar sa cup din hannun ta gaban ta Sannan ta bude kwallar , dumamen tuwan dawa ne da miyar kuka a ciki Hannu Hayat ta kai ta fara cin abincin ta cikin konciyar hankali Ta na tsaka da cin abincin ta inna ta ce ma ta " ya kamata ki daina yawwan fitar nan da ki ke yi , kin ga auren ki da Rabeh saura sati biyu " Slowly Hayat ta dago kai ta kali inna ta marairaice fuska ta ce " inna don Allah ki ma Adda magana wlh ba na son auren nan , kowa ya san cikin kauyen nan , Matar shi kulu ba ta da kirki " Cikin nitsuwa inna ta katse ta da cewa " Shahd dole ki yi hakuri , ko ni ba na son auren nan amma ba yadda zan yi , Addan ki ya rufe ido a kan maganar nan , ko jiya sai da mu ka samu sabani da shi a kan maganar nan " " yanzu inna ......... " Da sauri inna ta katse ta da cewa " Hayat ya isa haka ki ci abincin ki tun bai yi sanyi ba " Shiru Hayat ta yi ta juya ta ci gaba da cin abincin ta idanun ta na kawo ruwa , har sai da ta Kamala ta sha ruwa sannan ta dauki kayan ta meda su kitchen sannan ta fito ta nufi dakin da ta yi niyar shiga da farko Ita dai inna da ido kawai ta ke bin ta har sai da ta shiga cikin dakin TAღRIN ZღCIYA 💖🌺💍 ( RETღRN ) (ROMANTIC LUV STORY )💋🔥 ❤👑 ꪑꪖꪶꪶꪖƙỉ᭢ ꪖꪑꫀꫀꪹꪖꫝ ꪖꪉᦔꪮꪗꪶꪖꪗꫀ 👑❤ 𝗔.𝗞.𝗔 𝐀𝐍𝐈𝐒𝐇❥ 🕊💞 Wattpad : @bennybite Marubuciyar littafin TAURIN ZUCIYA EXILED PRINCE ( LOVE MEETS POWER ) TWO LIGHTS ( YAR JARIDA ) and now TAURIN ZUCIYA ( RETURN ) FOR MORE INFORMATION KU TABO WANNAN NUMBER +22798999753 WHATSAPP ONLY , Thanks 👍💕 اللَّهُمَّ صَلِّ عَلَى مُحَمَّدٍ وَعَلَى آلِ مُحَمَّدٍ، كَمَا صَلَّيْتَ عَلَى إِبْرَاهِيمَ وَعَلَى آلِ إِبْرَاهِيمَ، إِنَّكَ حَمِيدٌ مَجِيدٌ، اللَّهُمَّ بَارِكْ عَلَى مُحَمَّدٍ وَعَلَى آلِ مُحَمَّدٍ، كَمَا بَارَكْتَ عَلَى إِبْرَاهِيمَ وَعَلَى آلِ إِبْرَاهِيمَ، إِنَّكَ حَمِيدٌ مَجِيدٌ️ TAP THIS LINK TO JOIN MY WHATSAPP GROUP COMMETS SECTION 👇👇👇👇👇👇 https://chat.whatsapp.com/LWmuu0yv6C9DAhpdepDb4i DOMIN SAMUN BOOK DI NA DA GA FARKO ZA KU IYA ADDING CHANEL DI NA TA WANNAN LINK 👇👇👇👇👇👇 https://whatsapp.com/channel/0029VaGhJCqKmCPUvpvIJ80i 𝗧𝗔𝗣 𝗧𝗛𝗜𝗦 𝗟𝗜𝗞𝗘 𝗧𝗢 𝗝𝗢𝗜𝗡 𝗠𝗬 𝗣𝗢𝗦𝗧𝗜𝗡𝗚 𝗥𝗢𝗢𝗠 👇👇👇👇👇👇👇 https://chat.whatsapp.com/LepRstkGv3sDf8Jj4Gm054 _________________✦✦✦✦✦✦✦✦✦✦✦✦✦✦✦__________________ [ 🅿🅰🅶🅴̥ 3 ❤🔥 ] ▪ US ( WASHINGTON DC ) Misalin karfe 10 na safe Nihal ta na zaune cikin parlourn gidan ta na kallon Tv Ta na haka kawai sai ganin wata yar karamar yarinya ta shigo parlourn da gudu ta na fadin " Mamie , Mamie , Mamie " ta kai karshen ta na fadawa jikin Nihal Yarinyar fara ce tas kamar baturiya amma kallo daya za ka yi mata ka san jinin haoussawa ce , a shekaru ba za ta wuce 4 years ba , ta na sanye cikin wata gown pink colour mai mugun kyau Wani kyakyawan murmushi Nihal ta yi kafin ta dauki yarinyar ta daura ta saman cinyar ta ta na fadin " Haleen di na , shi ne ba ki fada min za ki zo ba " Yar siririyar dariya ta yi da Muryar nan ta ta irin ta yara Ta na shirin magana Ayna ta shigo parlourn ta na sallama dan kallo daya na yi mata na gane ta , Anas ne rai da rai babu ta inda ta baro shi sai wajen wadanan ash eyes na Zarah Cike da fara'a Nihal ta amsa mata sallamar ta kafin ta daura da cewa " ya mijin nawa ya ke ina ki ka baro shi " Yar karamar dariya Ayna ta yi ta na dan sunkuyar da kai ta ce " ya na nan mummy ya ce ma a gaishe ki " " Ina amsawa ki ce mishi na yi fushi tun dawowar ku da ga Turkey har yanzu bai zo gani na ba " Nihal ta fada ta na sauke Haleen da ga saman cinyar ta ta zaunar da ita geffen ta Dai'dai lokacin da Ummi ta fara sauko stair ta na sanye cikin doguwar riga mara nauyi fara kal , ta saki wannan curly hair din ta sak irin na Aylan ya zubo mata har saman shoulder ta na tafe kai a sunkuye ta na latsa wayar hannun ta Sai da ta karaso cikin parlourn sannan ta jiyo Muryar Ayna ta na fadin " Sannu Diyar Daddy " Da sauri Ummi ta dago kai ta kali Ayna , nan take ta saki wani cool murmushi ta bude hannayan ta ta nufi Ayna Mikewa Ayna ta yi ita ma ta nufe ta su ka rungume juna Ummi na fadin " Saukar yaushe , shi ne ba za ki kire ni ba " Raba jikin su Ayna ta yi su na rike da hannun juna su ka koma su ka zauna saman sofar da Ayna ta taso ta na fadin " na yi wajen three weeks fa da na dawo , ko ranar da na dawo sai da na zo gidan nan amma mummy kawai na tardo " Murmushi mai dan sauti Ummi ta yi kafin ta kali Haleen ta ce " Hi my baby girl , ba za ki gaishe da Aunty ba yau " Noke mata kafada Haleen ta yi ta na komawa jikin Nihal ta boye fuskar ta Yar karamar dariya Ayna ta yi kafin ta ce " ina ga ba yanzu ba za ku shirya ke da ita ba " Ummi na shirin magana Vedad ya sauko stair da gudu Iqbal na biye da shi ya na fadin " Vedad ka dawo ka ba ni waya ta " Karasowa cikin parlourn Vedad ya yi da gudu ya na dariya ya nufi Nihal ya zauna geffen ta ya na fadin " Mummy wlh shi da wata yarinya ya ke waya har da ce mata baby " Da sauri Iqbal ya nufe shi ya dunkule hannu ya kai mishi bugu a ciki Wata yar siririyar kara Vedad ya saki ya saki wayar ta fadi kassa ya ida shigewa jikin Nihal kamar baby Kamar da ga sama su ka jiyo Muryar Ash ya na fadin " Tun da kun yi breakfast , sai mu Hau training ko ? " A tare Vedad da Iqbal su ka juya su na kallon kofar shigowa parlourn Ya na tsaye ya rike hannayan shi a baya , ya na sanye da Trouser na Army da t-shirt Fara A hankali ya ke takowa ya karaso cikin parlourn kallon Nihal ya yi ya ce " Mummy , ku shirya gobe za mu Tafi Nigeria " " ban gane ba , ba cewa ka yi ba sai next week " Nihal ta fada Stair ya nufa ba tare da ya juyo ba ya ce " Vedad , Iqbal let's go " ya kai karshen ya na fara hayewa stair Kallon juna Iqbal da Vedad su ka yi kowa ne sai zaro idanu ya ke yi , sun san abun da Ash ya ke nufi da hakan " To sai ku tashi ku je tun bai dawo neman ku ba , laifin ya karu " Ummi ta fada ta na yi musu dariyar keta Mikewa tsaye Vedad ya yi ya na dan karamin tsaki ya fara takawa ya nufi stair ya na fadin " wlh in ya dake ni a kan ka zan rama " Bin bayan shi Iqbal ya yi zuciya na duka uku uku ya na tsoron a ce Ash ya ji abun da Vedad ya fada da ta shi ta kare yau Kai tsaye part din Ash su ka nufa A tare su ka yi sallama su ka shigo parlourn Ya na zaune saman sofa ya na rike da laptop din shi ya na latsa wa , cikin zuciyar shi ya amsa musu sallamar su dan ko lips din shi ba su motsa ba A hankali su ka karaso cikin parlourn tun kafin su ce wani abu ya ce musu " kneel down " Wasu yawu su ka hadiye kafin su karaso geffen shi su ka yi kneel down su ka daga hannayan su sama kai a sunkuye Sai da ya dauki wajen good 30 minutes a haka ba tare da ya dago ya kale su bare ya ce musu wani abu A hankali Vedad ya fara yi mishi kukan shagwaba ya na fadin " Big bro ni fa ko breakfast ban yi ba " Slowly Ash ya dago kai ya kale shi , cikin nitsuwa ya ce mishi " je ka kawo mana fruits " Bai gama rufe bakin shi ba Vedad ya tashi da gudu ya fice parlourn Hararrar kassan ido Iqbal ya yi mishi cikin zuciyar shi ya na fadin " Zan kama ka " Ash kuma ya na jin Vedad ya fita ya ce ma Iqbal " kai da waye ka ke waya " Dum ya ji gaban shi ya fadi har da zaro idanu Murya na kerma ya ce " ba..... ba kowa " Ajiye laptop din shi gefe Ash ya yi ya dago kai ya kali Iqbal ya matse gera ya ce " kariya za ka yi min " Da sauri Iqbal ya girgiza mishi kai " okay fada min da wa ka ke waya ko kuma mu tafi dakin horo " ya kai karshen ya na juyawa ya dauki laptop din shi ya ci gaba da abun da ya ke yi Wasu yawu Iqbal ya hadiye ya dan ja baya kadan lips din shi har kerma su ke yi ya ce " My girlfriend " ya kai karshen ya na lumshe idanun shi da karfi ya na jiran saukar naushi Gyada kan shi Ash ya yi kafin ya ce " She is muslim ? " A hankali Iqbal ya bude idanun shi ya kali Ash na dan second kafin ya ce " yes she is muslim , university din mu guda " " what is her name , da ga ina ta ke kuma " " Maya ! Yar kassar NEW YORK ce karatu ne ya kawo ta nan amma duk familyn ta su na NEW YORK " Shiru Ash ya yi bai ce mishi komai ba Sai da ya dauki wajen good five minutes kafin ya ce " okay ! " Ya na gama rufe bakin shi Vedad ya shigo dakin ya na sallama hannun shi rike da tray din breakfast din su , Fruits sai Pancakes da juice dan ya San Ash ba ya yin wani breakfast mai yauni Pancakes din ma kan shi ya dauko ma Kassa saman carpet ya ajiye tray din sannan ya zauna shi ma , ko jiran wanda ya aike shi bai yi ba ya dauki fork da knife ya fara cin Pancakes din shi " let's go eat " ya fada wa Iqbal ba tare da ya kale shi ba Jinjina mishi kai ya yi kafin ya sauke hannayan shi ya matso kusa da Vedad ya fara shan fruits shi kuma cikin zuciyar shi ya godewa Allah da Ash bai mishi komai ba Sai da ya Kamala aikin da ya ke yi sannan ya ajiye laptop din shi gefe sannan ya sauko kassa shi ma ya fara shan fruits Ya na zama Vedad ya yanko pancake ya hada da strawberry ya kai fork din saitin bakin Ash ya na murmushi Ba musu Ash ya bude baki ya karba dai'dai lokacin da junior ya turo kofar dakin ya na sallama A tare Vedad da Iqbal su ka dago kai su na amsa sallamar shi , shi kuma Ash cikin zuciya ya amsa Dan karamin murmushi ya saki ya na karasowa cikin dakin ya na fadin " Meeting a ke yi ba a gayato ni ba " ya kai karshen ya zama geffen Ash Yar karamar dariya Vedad ya yi kafin ya ce " Marshal , ba wata Meeting breakfast ne kawai mu ke yi " Hannu junior ya kai ya dauki Apple ya na fadin " breakfast a karfe 11 ba dan mintina , sai dai ka ce karawa ku ke yi " Mikewa tsaye Ash ya yi ya dauki laptop din shi ya juya ya shiga bedroom din shi Mikewa shi ma junior ya yi ya bi bayan Ash ya na fadin " ina zuwa " Da to su ka amsa mishi a tare kafin Vedad ya ce ma Iqbal " mu je mu yi video game " Hararrar wassa Iqbal ya yi mishi ya na fadin " kai ba ka da aiki sai game ba ka da exams ne " Kashe mishi gera guda Vedad ya yi ya na fadin " injustice ? " Da sauri Iqbal ya ce " ina son Superman " Yar karamar dariya Vedad ya yi ya na tashi da Da sauri shi ma Iqbal ya tashi ya bi bayan shi su ka bar part din da gudu , su ka bar kayan breakfast din a nan Bangaran su Ash kuma , junior na shigowa bedroom din ya isko Ash zaune bakin gadon ya na ci gaba da aikin shi cikin laptop Geffen shi Junior ya karaso ya zauna ya na kallon abun da Ash ke yi cikin laptop din shi Yar karamar dariya junior ya yi ya na dafa shoulder din Ash ya ce " kar ka ce min General of American Army Staff Ash har ya fada tarkon soyayya " Dan karamin tsaki Ash ya yi kafin ya kauda kan shi gefe sannan ya ce " har ka gama shirya wa tafiyar mu ne ? Gobe za mu tafi " " kar ka damu General ni ko yanzu ne sai mu tafi , amma kai ka na da aiki gaban ka sai a je a rarrashi madam tun lokaci bai kure ba " ya kai karshen ya na bushe wa da dariya Dan tsaki Ash ya yi ya kai hannu ya dauki pillow da ke geffen shi ya tila ma junior a fuska ya na fadin " girlfriend din Iqbal ce , ina son na samu karin bayani a kan ta idan mun dawo da ga Nigeria , zan sa his excellency ya je neman mishi auren ta " " okay that's good , to kai fa yaushe za a auren na ka " Wani dogon nunfashi Ash ya ja sannan ya ajiye laptop din shi saman bedside drawer ya juyo ya kali junior ya ce " duk ranar da ka yi aure , a ranar za a yi na wa " ya na gama fadar haka ya tashi ya nufi dressing room Da kallo Junior ya raka shi har sai da ya shiga sannan ya sa hannu da sauri ya dauki laptop din Ash ya yi wasu dane dane kafin ya meda ta ya ajiye ya tashi ya fice bedroom din Ya na fitowa parlourn ya ga tray din breakfast da su Vedad su ka bari Dan karamin tsaki ya yi kafin ya karaso wajen tray din ya duka ya dauke shi sannan ya fice part din Kai tsaye Stair ya sauko , tun da ya daura ido kan Ayna ya saki wani kyawatencen murmushi , haka zalika ita ma murmushi ta yi mishi cikin tsokana ta ce " Marshal Junior , ashe ka na nan " dai'dai ya ida sauko stair din Dan karamin murmushi ya yi ba tare ya ce mata komai ba ya nufi dining room ya ajiye tray din hannun shi saman table din sannan ya juyo ya koma cikin parlourn ya nufi geffen Ayna ya zauna sannan ya rage sautin Muryar shi kassa kassa ya ce mata " ki na ji ko , ki daina kira na da Marshal junior , na san ba za ki iya kiran suna na kai tsaye ba , dan haka ki ce Marshal kawai , ai duk ni ne " Yar karamar dariya Ayna ta yi , Ummi kuma ta kauda kai gefe dan yanayin face din ta ya sauya ta ji abun da ya ce hakan ya so ya dan sosa mata rai Shi kuma ko a jikin shi ya na gama fadar haka ya sa hannu cikin aljihun shi ya ciro wayar shi ya fara latsawa Ba su yi one minute ba wani jibgegen soji ya shigo parlourn , ya na sanye da trouser din shi na soja da T-shirt fara Kai tsaye junior ya nufa ya sara mishi cikin girmamawa ya ce " good morning Sir " Ba tare da ya dago kan shi ba ya ce ma sojan nan " okay Felix ! Je ka gyara part din General sannan ka shirya min kaya na , an sauya magana gobe za mu tafi Nigeria " " Yes sir " wanda ya kira da Felix ya fada ya na sara mishi sannan ya juya ya nufi Stair ya Haye ya nufi part din Ash Ya na barin wajen Ayna ta mike ta na fadin " Mummy , ni zan koma gida , Haleen tasso ko " " ayya har za ki koma , Tom shikenan ki gaishe da mijin na wa in kin koma " Nihal ta fada cikin sanyi Da sauri Haleen ta mike tsaye saman sofar ta kai dan bakin ta saitin kumatun Nihal ta mata kiss ta na fadin " See you Next time mamie " da ga haka ta diro da ga saman sofar ta nufi Ayna da gudu ta na yar dariya Riko hannun ta Ayna ta yi sannan ta juya ta kali junior ta riko gashin shi da hannu daya har sai da ya saki yar kara ya na fadin " please let me , me kuma na yi miki " " yi min shiru , wlh ka tabbatar kafin ka dawo da ga Nigeria , ka samo mana sirika " " Ayna ni kadai ki ka raina wlh , in haka ne ki je ki yi wa Ash hakan , ai shi ma ya isa aure " " ba ruwan General a nan , ni kai na sani , wlh in ka dawo a tuzuru to sai na yi maka auren dole , ga Ummi a gida , na san za ta bada hadin kai a fitar da brother din ta kunya " ta kai karshen ta na sakin gashin shi ta saki yar dariya " a'a Ayna gaskia Junior di na ya fi karfin Ummi " Nihal ta fada ta na kallon Ummi ta kassan ido Murguna ma ta baki Ummi ta yi ba tare da ta ce komai ba " mummy sai an jiman ku " Ayna ta fada ta na fara takawa za ta bar parlourn A tare Junior da Nihal su ka daga murya su na fadin " ki gaishe da gida " Da to ta amsa musu ta na sa kai ta fice war ta Ta na fita Nihal ta kali Ummi ta ce " yanzu Ummi ba za ki raka ta ba " " zuwa ina ? " Ummi ta fada cikin ko in kula kafin ta mike ta fara takawa ta Haye stair abin ta Da kallo Junior da Nihal su ka rakata , har sai da ta Haye sannan ya ida konta wa saman sofar ya na ci gaba da latsa wayar shi Ya na a haka ya jiyo Muryar Nihal ta na fadin " Junior , wai yanzu kai ma Ash za ka bi ku mutu a tuzurai kenan , ba ka da aiki sai latsa waya " A hankali ya juyo ya kali Nihal ya saki wani dan karamin murmushi ya ce " mummy , ni fa ina son na yi auren , matar ce wadda ba ke so , she is not muslim kin ga ba zan iya auren ta ba , shi kuma Ash ba matar ba ce bai samu ba , sam sha'awar mace ce ba ya yi , kar ki so ki ga yan matan da ke bin shi har headquater da sunnan su na son shi da ga musulman har krista , wlh akwai yarinyar da ta baro UK kawai dan ta gan shi , kuma yarinyar president din UK ce fa, ko last week sai da ya sa wata officer ta yi wa wata yarinyar dukan tsiya kawai dan ta rungume shi , kar ki so ki gani har yanzu yarinyar ta na Asibiti " Dan karamin murmushi Nihal ta yi ta na dan sunkuyar da kai cikin zuciyar ta ta ce " dole mata su so shi , mahaifin shi ma haka ya ke farin jini wajen yan mata " ba ta kai karshen maganar ta ba idanun ta su ka ciko da hawaye , da sauri ta tashi ta koma part din ta Shi dai Junior da kallo ya rakata har sai da ta shiga sannan ya mike zaune ya na shirin tashi , Vedad da Iqbal su ka sauko stair a guje Dan karamin tsaki ya ja cikin ranshi ya ce " yaran nan wlh horon soja zai dace da ku " ya na gama fadar haka ya dago ya kali su Vedad dai'dai sun karaso cikin parlourn ya daka musu ya na fadin " Vedad, Iqbal mazza ku zo nan " Cak su ka tsaya da gudun su , su na dan zaro idanu su na kallon shi , sun san halin junior ba karamin maketaci ba ne , musaman in ba ya gaban idon Ash Wasu yawu su ka hadiye a tare kafin su daga kafa su ka nufe shi Tun kafin su karaso ya nuna musu gaban shi da yatsa allamun su yi kneel down Ba musu su ka karaso gaban shi su ka yi kneel down , Vedad sai turo dan bakin nan na shi ya ke ya na shagwabe fuska Sai da junior ya dauki wajen good ten minutes ya na kare musu kallo ya na daure fuska sannan ya ce musu " wai ku ba ku iya zama waje guda ba , yanzu fada min , gudun me ku ke yi haka sai ka ce wasu babys " Vedad ne ya amsa mishi da cewa " Marshal ba Iqbal ba ne , video game ne mu ke yi , kawai sai ya daura bet wai duk wanda ya yi winnig , loser zai ba shi 1000$ kuma ni fa ban da kudi , shi ne da ya yi winnig ya ce sai na ba shi kudin shi ko ya dake ni , shi ne na gudo " ya kai karshen cikin shagwaba Kamar da ga sama su ka jiyo Muryar Ash ya na fadin " ba na hana ku yin bet ba " Dum Vedad da Iqbal su ka ji zuciyoyin su sun yi muguwar faduwa , har wasu fitsari Iqbal ya ji sun taho mishi Ash kuma tsaye ya ke bayan su ya rike hannayan shi a baya , ya na sanye da Trouser Black colour da T-shirt white colour , ya daure wannan darck black curly hair din na shi a baya sai tashin kamshi ya ke yi kamar wanda ya yi wankan turare Wasu yawu Iqbal ya hadiye har hawaye su ka zubo mishi ya san yau tashi ta karre laifi biyu rana guda ya san yau sai ya yi jinya word room Wata razananiyar tsawa ce Ash ya daka musu , ba su Vedad ba har shi junior sai da ya sha jinin jikin shi ya na zaro idanu " Marshal kai min su dakin horo ina zuwa " ya fada ya na juyawa ya nufi part din Nihal Da kallo su ka raka shi sai da ya shiga sannan Iqbal ya saki wani marayen kuka kamar karamin yaro ya na fadin " wayooo na shiga uku ni Iqbal , Vedad Allah ya isa tsakani na da kai , yanzu za ka janyo min " Bai gama rufe bakin shi ba junior ya mike tsaye ya fara takawa ya nufi door din fita parlourn ya na fadin " zauna nan ka na kuka ya tardo ku , wlh sai na lahira ya fi ku jin dadi " Ai bai gama rufe bakin shi ba su ka tashi da gudu su ka bi bayan shi su ka fice parlourn Bangaran Ash kuma , a hankali ya shiga part din Nihal ya na sallama cen kassa kassa Kai tsaye bedroom din ta ya wuce , ya na shiga ya isko ta zauna kassa ta jingina a jikin gadon ta kamar wata yarinya ta na kuka ga pics din Aylan duk zube a gaban ta Bai ce mata komai ba ya karaso gaban ta , ya duka duk ya kwashe pics din nan ya bude box din bedside drawer ya saka su a ciki sannan ya koma geffen Nihal ya zauna a kassa shi ma ya na kallon gaban shi bai ce mata komai ba A hankali ta fara rage sautin kukan ta , ta na sa hannu ta goge hawayen ta , ta gyara zaman ta , ta yi irin zaman cin tuwo Sannu sannu har ta daina kukan baki daya Ash bai ce mata komai ba , ko kifta idanu bai yi ba Sai da su ka share wajen 30 minutes a haka ba wanda ya ce ma wani ufan A hankali Ash ya bude baki ba tare da ya juyo ba ya ce " mummy , na gaji da ganin ki cikin wannan halin , duk fa abun da ki ke yi ina sane da shi , impossible ne a ce rana guda ta wuce ba ki yi kuka ba ko da cikin dare ne , wani lokaci cikin barcin ki , ki ke yin kukan , Why mummy ? A ganin ki in ya san halin da ki ke ciki zai ji dadi ? Mummy you know , you are my power , you are my weakness and you are my happiness , duk lokacin da na gan ki cikin farin ciki ko ban nuna ba , cikin zuciya ta ina farin ciki , please mummy ki daina cutar da kan ki haka , ke kadai ki ka rage min a duniya don Allah kar ki jawa kan illar da za ta raba ni da ke " Wani cool murmushi Nihal ta saki ta na daura hannun ta saman kan shi , a hankali ta dan sunkuyo da kan shi ta mana mishi kiss a goshi ta na fadin " shikenan my little , duk yadda ka so haka za a yi amma ina da sharadi " Slowly ya juyo da kan shi ya daga mata gera allamun miye sharadin ? Kara fadada murmushin ta ta yi kafin ta ce " ina son ka yi aure ka ga in ina ganin jikoki na zan rage wannan yawwan damuwar " " ba banza ba Daddy ke cewa ki na yi mishi wayo " Ash ya fada ya kokarin mikewa Da sauri ta riko hannun shi ta medo shi ya zauna ta na yar dariya ta kai hannu ta ja hancin shi ta ce " shi dai ya ke min wayo , yanzu maganar auren ka ? " " soon " ya fada a takaice Hararrar wassa ta yi mishi kafin ta ce " wlh ka fitar da matar aure idan mu ka je Nigeria ko kuma na yi maka irin yadda papi din ku ya yi mana , kawai sai jin na yi ya aura min Daddyn ku " ta kai karshen ta na sakin hannun shi Mikewa tsaye ya yi ya yi taku biyu gaba sannan ya tsaya ya dan juyo da kan shi ya ce " mummy duk duniyar nan babu matar da ta kai na bude baki na ce ina son ta bayan ke , zancen aure kuma gwara ki bar shi dan ba zan taba yi ba " ya na gama fadar hakan ya sa kai ya fice Da kallo ta raka shi har sai da ya fita sannan ta yi yar karamar dariya ta ce " yaro man kaza, ba ka san wuta ba sai ka taka , ni na ke da iko da kai ba kai je da iko da ni ba , Allah ya kai mu Nigeria wlh da matar ka za ka dawo ko ka ki , ko ka so zamu gani " ta na gama fadar haka ta sake bushewa da wata shegiyar dariya irin ta mugun ta ▪ASH 🔥 Bayan ya baro part din Nihal kai tsaye part din shi ya koma , allamun ya manta da Su Vedad Bayan ya shiga bedroom din shi a parlourn ya zauna saman sofa three seaters ya fido wayar shi da ga cikin aljihu ya fara latsawa Bai fi five minutes ba da zama ya , Felix ya shigo parlourn ya na dauke da wasu bucket biyu na ruwa wanda a kila za su kai 30 liter na ruwa Gaban shi Felix ya ajiye bucket din nan sannan ya sara mishi ya fice dakin , dai'dai lokacin da Junior ka shigo dakin Vedad da Iqbal na biye da bayan shi Cikin dakin Junior ya karaso ya zauna saman sofa geffen Ash ya ce ma su Vedad su karaso ciki Wasu yawu su ka hadiye kafin su ka karaso gaban shi su yi kneel down Ba tare da ya dago kan shi ba Ash ya ce musu su shanye ruwan da ke cikin bucket din nan Ba karamin zaro idanu Vedad da Iqbal su ka yi ba su na kallon bucket din gaban Ash , ai ko cikin kwana guda ba su iya shanye ruwan nan " idan har ku ka bari na sake maimaita abun da na ce " Ash ya fada ba tare da ya dago kan shi ba Nan take kuka ya kubce wa Vedad kamar baby har da shagwaba ya na fadin " Big bro don Allah ka yi hakuri wlh ba zan sake ba , duk Iqbal ne shi ya ce mu yi bet din ai , ni ban da kudi wlh " ya kai karshen ya na kara sautin kukan shi Ya na gama rufe baki shi ma Iqbal ya shiga yin kuka ya na fadin " I'm sorry big bro ba zan sake ba " Slowly Ash ya dago kai ya zuba musu wadanan sexy blue eyes din na shi , sai kuka su ke yi , Vedad har da majina ya na hadiyar zuciya Shi kuma junior sai kumshe dariya ya ke , ya samu mugun ta ( munafiki ko shi ne a ka ce ya shanye fiye da liter goma ta ruwa lokaci guda ba zai iya ba , har da yi musu dariya 😑😑😑😑 ) Ajiye wayar shi gefe ya yi kafin ya mika wa Vedad hannu a kan ya zo Da sauri Vedad ya matso gaban shi , ya na ci gaba da kukan shi Hannu Ash ya kai ya kamo kunnen shi ya murde ya na fadin " nan gaba ko game za ku yi kar ku daura bet , na san ba yau ba ku ka fara , to yau shi ne na karshe in na sake kama ku da irin wannan laifin " ya na gama fadar haka ya saki kunnen Vedad , sannan ya kali Junior Gyada mishi kai Junior ya yi kafin ya mike ya nufi table din da ke kassan makekiyar Tv plasma din parlourn ya dauko kwallin handkerchief ya dawo ya zauna saman sofar ya mikawa Ash Hannu ya sa ya zaro handkerchief biyu sannan ya shiga gogewa Vedad hawayen shi , sai da ya goge mishi sannan ya ce ya tashi ya je ya sha fruits din shi , Ai ko da sauri Vedad ya tashi ya fice parlourn Ya na fita Ash ya mike ya nufi bedroom din shi ya na ce ma Iqbal ya biyo shi Ba musu Iqbal ya tashi ya bi bayan shi a hankali kamar wanda a ka yi wa dole ( ko da ya ke dolen ce a ka yi mishi 🤣🤣🤣 ) Bayan sun shiga bedroom din , zama Ash ya yi bakin gadon shi , shi kuma Iqbal ya yi tsaye gaban shi ya sunkuyar da kai sai jan majina ya ke yi " dauko min waya ta " Ash ya fada mishi ya na kai hannu ya dauki laptop din shi da ke saman bedside drawer , shi kuma Iqbal ya juya ya koma parlourn babu kowa junior ya yi tafiyar shi , dauko wayar Ash da ya bari saman sofa ya sannan ya koma bedroom din ya ajiye ta saman bedside drawer ya koma gaban Ash ya yi tsaye TAURIN ZUCIYA 💖🌺💍 ( RETURN ) ( ROMANTIC LOVE STORY )💋🔥 ❤👑 MALLAKIN MEERAH 👑❤ اللَّهُمَّ صَلِّ عَلَى مُحَمَّدٍ وَعَلَى آلِ مُحَمَّدٍ، كَمَا صَلَّيْتَ عَلَى إِبْرَاهِيمَ وَعَلَى آلِ إِبْرَاهِيمَ، إِنَّكَ حَمِيدٌ مَجِيدٌ، اللَّهُمَّ بَارِكْ عَلَى مُحَمَّدٍ وَعَلَى آلِ مُحَمَّدٍ، كَمَا بَارَكْتَ عَلَى إِبْرَاهِيمَ وَعَلَى آلِ إِبْرَاهِيمَ، إِنَّكَ حَمِيدٌ مَجِيدٌ❤️ BISMILLAHIRRAHMANIRRAHIM PAGE 4 ❤🥂 TAღRIN ZღCIYA 💖🌺💍 ( RETღRN ) (ROMANTIC LUV STORY )💋🔥 ❤👑 ꪑꪖꪶꪶꪖƙỉ᭢ ꪖꪑꫀꫀꪹꪖꫝ ꪖꪉᦔꪮꪗꪶꪖꪗꫀ 👑❤ 𝗔.𝗞.𝗔 𝐀𝐍𝐈𝐒𝐇❥ 🕊💞 Wattpad : @bennybite Marubuciyar littafin TAURIN ZUCIYA EXILED PRINCE ( LOVE MEETS POWER ) TWO LIGHTS ( YAR JARIDA ) and now TAURIN ZUCIYA ( RETURN ) FOR MORE INFORMATION KU TABO WANNAN NUMBER +22798999753 WHATSAPP ONLY , Thanks 👍💕 اللَّهُمَّ صَلِّ عَلَى مُحَمَّدٍ وَعَلَى آلِ مُحَمَّدٍ، كَمَا صَلَّيْتَ عَلَى إِبْرَاهِيمَ وَعَلَى آلِ إِبْرَاهِيمَ، إِنَّكَ حَمِيدٌ مَجِيدٌ، اللَّهُمَّ بَارِكْ عَلَى مُحَمَّدٍ وَعَلَى آلِ مُحَمَّدٍ، كَمَا بَارَكْتَ عَلَى إِبْرَاهِيمَ وَعَلَى آلِ إِبْرَاهِيمَ، إِنَّكَ حَمِيدٌ مَجِيدٌ️ DOMIN SAMUN BOOK DI NA DA GA FARKO ZA KU IYA ADDING CHANEL DI NA TA WANNAN LINK 👇👇👇👇👇👇 https://whatsapp.com/channel/0029VaGhJCqKmCPUvpvIJ80i TAP THIS LINK TO JOIN MY WHATSAPP GROUP COMMETS SECTION 👇👇👇👇👇👇 https://chat.whatsapp.com/LWmuu0yv6C9DAhpdepDb4i 𝗧𝗔𝗣 𝗧𝗛𝗜𝗦 𝗟𝗜𝗞𝗘 𝗧𝗢 𝗝𝗢𝗜𝗡 𝗠𝗬 𝗣𝗢𝗦𝗧𝗜𝗡𝗚 𝗥𝗢𝗢𝗠 👇👇👇👇👇👇👇 https://chat.whatsapp.com/LepRstkGv3sDf8Jj4Gm054 _________________✦✦✦✦✦✦✦✦✦✦✦✦✦✦✦__________________ [ 🅿🅰🅶🅴̥ 4 ❤🔥 ] dauko wayar Ash da ya bari saman sofa ya yi sannan ya koma bedroom din ya ajiye ta saman bedside drawer ya koma gaban Ash ya yi tsaye , ya sunkuyar da kai Cikin nitsuwa Ash ya dago kai ya kali Iqbal sannan ya ce " na san dalilin da ya sa ka yi bet din nan , next time in ka na bukatar kudi ka taho ka fada min , sannan wannan kukan da ka ke yi kamar Vedad ka daina shi , ba girman ka ba ne , idan mu ka dawo da ga Nigeria za ka fara karbar horon soja " Gyada kan shi Iqbal ya yi bai ce komai ba , har ga Allah ba ya son zama soja amma tun da Ash ya ce zai fara ba shi horon soja babu wanda ya isa ya hana shi Ya na haka ya ji wayar shi da ke ciki trouser din shi ta yi ruri Shi ya ma manta da Ash na gaban shi kawai ya kai hannu ya ciro wayar da ga cikin aljihun shi ya na duba text din da ya shigo , nan ya ga One hundred Millions of Dollars da Ash ya turo mishi cikin account din shi Bai san lokacin da ya saki wani kyawatencen murmushi mai sauti ya nufi Ash da gudu ya rungume shi ya na fadin " Thanks a lot my big bro " " okay sake ni yanzu " Da sauri Iqbal ya sake shi ya na fadin " Sorry sorry " Kallon shi da kyau Ash ya yi kafin ya kai hannun shi ya yi mishi dan karamin mari ya na fadin " nan gaba ka fara tabbatar ka na da kudi kafin ka yi mata alkawarin fita shan ice cream , duba cikin dayar bedside drawer akwai Cash ka dauki wanda zai isar ka " Kara fadada murmushin shi Iqbal ya yi da sauri ya tashi ya nufi dayar bedside drawer ya zauna bakin gadon ya bude box na farko , cike ya ke makil da dollars bandir bandir a jere tsab , ko ni sai da na hadiye yawu Cike da zalama Iqbal ya kai hannu ya fara debar kudin nan , akkila sai da ya dauki wajen bandir goma kafin ya rufe box din ya taso ya dawo gaban Ash ya dan sunkuyar da kai ya manna mishi kiss a kumatu ya na fadin " na gode big bro " " in ka wuce karfe 8...... " Da sauri Iqbal ya katse shi da cewa " karfe 6 ina cikin gidan nan ba za mu jima ba " da ga haka ya sa kai ya fice part din baki daya ya koma part din shi Da kallo Ash ya raka shi sai da ya fita , har ga Allah ya na mutuwar son ganin yan uwan shi cikin farin ciki , duk lokacin da ya gan su cikin farin ciki ji ya ke ba ya da bukatar wata mace a kusa da shi in har zai ci gaba da ganin su a haka Ko yanzu kawai dan ya ba su tsoro ne ya ce su shanye ruwan nan , amma shi da kan shi ya san ba za su iya ba , amma ba ya son su na yin bet , ya san kuma ba wanda ke kawo shawarar nan , sai Iqbal , dan shi Vedad wani sha tara ne , duk Nihal ta tsangarta shi , in ya na son kudi kai tsaye ya ke tambayar shi ba ya jin tsoro , Iqbal nai de ko ya na son kudi sai dai ya je wajen Nihal ko Ummi dan ya san ba za su tambaye shi ba me zai yi da kudin , Ash kuma sai ya yi mishi tambaya fiye da goma , Iqbal na fita ya dauki laptop din shi ya ci gaba da aikin shi Shi kuma Iqbal ya na baro part din shi kai tsaye ya koma , ya na shiga ya wuce toilet ya yi wanka , ya fito ya shirya cikin trouser white colour da t-shirt navy blue , ya daura wata jacket White color , kafafun shi kuma cikin wasu sneakers Navy blue ma su mugun kyau sai tashin kamshi ya ke , ya yi kyau over , a haka ya sa kafa ya baro cikin gidan , ya nufi parking space ya shiga wata dankareriar mota Fara kal , har wani kyali ta ke yi na daukar ido sannan ya bar gidan da mugun gudu Ya dauki wajen Good ten minutes ya na driving kafin ya iso bakin wani makeken Building na apartments , Building din ya na da girma sosai a killa zai kai hawa 100 Ya na isowa Bakin kofar shiga Building din ya yi parking din motar ya dauki wayar shi ya rubuta text sannan ya meda ta ya ajiye ya hada kan shi da steering motar Bai fi five minutes wata Kyakyawar budurwa ta fito da ga cikin building din ta karaso wajen motar ta nufi bangaran mai zaman banza ta bude ta shiga , ta na sallama kassa kassa Yarinyar kyakyawa ce ba laifi a shekaru za ta kai 20 years haka , amma da ga gani ba cikakiyar baturiya ba ce , fara kal da ita amma duk da farin ta Iqbal ya fi ta dan Haske , ta na sanye cikin wata Gown white colour har kassa mai mugun kyau ta sha ruwan stone , ta yi Rowling veil din ta navy blue a kai , ta yi simple make up , abun dai Masha Allah Ya na jin ta rufo kofar motar ya dago kan shi slowly ya juyo ya kale ta Wani kyawatencen murmushi ta saki ta na daga mishi gera guda Dan karamin murmushi ya yi kafin ya ce " kin yi kyau gaskia " Hararrar wassa ta yi mishi ta na kauda kai gefe wai ita ta ji kunya Yar karamar dariya ya yi kafin ya tada motar su ka bar wajen ya na fadin " Baby ina ki ke son mu je " Dawo da kallon ta ta yi gare shi cikin nitsuwa ta ce mishi " Duk inda ka ke so , amma ya kamata mu koma gida kafin karfe 7 , gobe ina da exams " Gyada kan shi ya yi ba tare da ya ce mata komai ba Ita dai kallon shi kawai ta ke ta na sakin murmushi Cen kuma sai ta bude baki a hankali ta ce mishi " na yi kewar ka sosai in ka tafi " Wani cool murmushi ya saki kafin ya yi parking din motar shi geffen titi ya juyo da kai ya kale ta , duk yanayin face din ta ya sauya ta marairaice fuska kamar za ta yi kuka " ya isa haka kar ki ce za ki yi min kuka , ni ma ba a son rai na ba zan yi tafiyar nan , kuma ai zan dawo " Shagwabe fuska ta yi ta na kauda kai gefe ta ce " ni na san da ka je za ka manta da ni , ka yi sabuwar Girlfriend a cen " Maganar ba karamar dariya ta ba shi ba , amma sai ya yi dan karamin murmushi ya zagayo da hannun shi a kugun ta , ya janyo ta jikin shi ya na kallon face din ta ya ce " ke din ma da ya ki ka sace zuciya ta , ba na tunanin bayan ke wata za ta iya " Yar karamar dariya ta yi ta kara matso da face din ta kusan ta shi " da gaske ba za ka so wata bayan ni ba ? " ta fada cike da shagwaba Gyada mata kai ya yi allamun eh " you promise ? " " I promise Mrs Iqbal " ya fada ya na kashe mata ido guda Yar karamar dariya ta yi kafin ta kai dan bakin ta ta daura lips din ta saman na shi ta yi mishi kiss Ta na shirin janye bakin ta ya cabko lips din ta na kassa ya ci gaba da kissing cikin kwarewa , nan take duk wata sigar jikin shi ta mike , ya zagayo da dayan hannun na shi a baya ta ya na shafawa a hankali Mayar mishi da martani ta shiga yi ita ma , dama ta jima ta na sha'awar shi amma kullum ya ki ba ta dama , yau dai ta samu abun da ta ke so A hankali ta kai hannu ta riko zip din jacket din shi ta fara yi kassa da shi har ta fida shi , sannan ya sa hannu ta cikin t-shirt din shi , maimakon ta yi sama kawai sai ta yi kassa ta na neman sa hannun ta cikin trouser din shi Ai ko cak ya damko hannun ta ya na ware idanun shi da su ka yi jazir , sai cikin na ta Slowly ya zame bakin shi da ga cikin na ta , cikin wata zazzakar murya ya ce mata " me ki ke shirin yi ? " A hankali ta girgiza mishi kai ta bude ta ce " I'm sorry , ni ma ban san na yi ba " Bai ce mata komai ya janye hannun ta , ya daura shi saman cinyar sa , sannan ya sa hannu ya Meda zip din jacket din shi , ya tada motar shi su ka bar wajen Marairaice fuska ta yi kamar za ta kuka ta ce " Baby , i'm sorry " Slowly ya juyo ya kale ta kafin ya saki wani cool murmushi ya riko hannun ta , ya kai shi saitin bakin shi ya yi mata kiss sannan ya ce " It's okay , za ki je Funfair ? " Da sauri ta gyada mishi kai ta na murmushi , shi ma murmushi ya yi mata da ga haka ba wanda ya sake cewa komai har sai da su ka isa wani makeken park , ba sai na fada muku na wanene ba A haka su ka shiga cikin park din nan , su na rike da hannun juna gwanin burgewa , park din ya na da mugun girma , sai misalin karfe 6 su ka baro shi , a hakan ma ba su hau duk carousel din park din Kai tsaye apartments din ta ya meda ta , a wannan karan sai da ya sauko ya raka ta har apartments din ta , su ka yi sallama ta masoya sannan ya baro building din ya koma gida kai tsaye Ya na komawa a ka fara kiran Sallar magriba , kai tsaye part din shi ya wuce dan babu kowa a parlourn , ya na shiga ya wuce toilet ya yi wanka ya fito ya shirya sannan ya yi sallat ▪AFTER SOME HOURS ▪ASH 🔥 Zaune ya ke saman bed din shi da ga shi sai short da singlet , ya rike da laptop din shi ya na faman aiki , allamun tun bayan fitar Iqbal bai je ko ina ba Ya na a haka Vedad ya shigo Dakin ya na sallama , ya na sanye da kayan barcin shi white color sai tashin kamshi ya ke yi , ya na rungume da wani pillow a kirjin shi , kai tsaye bed din Ash ya nufa ya Haye ya yi rub da ciki Sarai Ash ya lura da shi amma bai ce mishi komai ba Sai da ya Kamala aikin shi sannan ya ajiye laptop din saman bedside drawer , ya kali Vedad ya daura hannun shi saman kan shi ya shiga shafa lalawsan gashin kan shi ya na fadin " My angel , what's wrong ? " " Let me , ni ba na son yi maka magana yau " ya fada ba tare da ya dago kan shi ba Ci gaba da shafa kan shi Ash ya yi ya na fadin " Why ? Laifin me kuma na yi ? " Bai gama rufe bakin shi ba rufe bakin shi ba Iqbal ya shigo bedroom din ya na sallama ya nufi Sofar da ke fuskantar bed din ya zauna ya na kallon su Vedad Ya na zama ya saki wata yar karamar dariya ya ce " Cutie pie , yau yan shagwabar ne ke sama ? " ya fada cike da tsokana Da sauri Vedad ya dago ya mike zaune ya tila wa Iqbal pillown hannun shi ya na fadin " Stop calling me Cutie pie " Da sauri Iqbal ya cabko pillown ya na dariya " ya isa in wassan ku , ku ke son yi , ku tashi ku fice min daki " Ash ya fada cikin tsare gida Turo dan bakin nan na shi Vedad ya yi cike da shagwaba ya ce " ni babu inda zan je a nan zan kwana ma " ya kai karshen ya na komawa geffen Ash ya zauna ya kontar da kan shi saman shoulder din Ash Shi dai Iqbal dan karamin murmushi ya yi kafin ya jingina bayan shi a jikin sofar ya daga kai sama ya lumshe idanun shi ya tafi duniyar tunanin shi Ash na ganin hakan ya kai hannu ya dauki laptop din shi zai ci gaba da aikin shi Vedad na ganin wallpaper din shi ya kai hannu ya kwace mishi laptop din ya na ci gaba da kallon wallpaper din ya saki wani kyawatencen murmushi " My angel are you okay ? " Ash ya fada dan ya ji kamar Vedad ya yi sanyi Girgiza mishi kai Vedad ya yi allamun ba komai ya na kashe laptop din ya mikawa Ash kayan shi Karba ya yi ya meda ta saman bedside drawer sannan ya kai hannayan shi ya talabo face din Vedad nan ya ga hawayen da ke konce cikin idanun shi Cikin konciyar hankali Ash ya ce mishi " My angel , why did you cry ? You know i don't like see you crying " A hankali Vedad ya sunkuyar da kan shi ya fada jikin Ash ya rungume shi da kyau murya kassa kassa kamar me kuka ya ce " Big bro , wlh ina kewar Daddy over , kullum da dadare sai na jira shi , ya zo ya yi min adu'ar barci , amma kullum ba ya zowa har barci ya dauke ni " " it's enough now , kar ka yi min kuka , ai ina nan , kuma Mummy ta na nan , ga Ummi and your best friend Iqbal , we are all here with you " " i know but ....... " Cikin nitsuwa Ash ya katse shi da cewa " But what , ko duk ba mu ishe ka ba ? " Nan take kuka ya kubce wa Vedad , cikin kukan ya ke fadin " but i want to see my Daddy , I missed him " Murya cike da rauni Ash ya ce mishi " please My angel stop crying , ni ma ina kewar Daddy over , kullum cikin yi mishi adu'a na ke , kai ma adu'a ya kamata ka dinga yi mishi duk lokacin da ka tuno da shi , ba kuka ba " Slowly Vedad ya dago da ga jikin Ash ya na fadin " Da gaske ka na kewar Daddy ? " ya fada ya kallon Ash cikin ido Gyada mishi kai Ash ya yi kafin ya kai hannayan shi ya fara goge wa Vedad hawayen shi ya na fadin " ina kewar shi mana , kawai dai na san adu'a ta ita ya fi bukata a yanzu , shi ya sa na shanye abun da ke cikin zuciya ta , ina yi mishi adu'a duk lokacin da na yi sallat " Dan karamin murmushi Vedad ya yi ya na fadin " Ni ma kullum in na yi sallat sai na yi mishi Adu'a " " Haka ya kamata ka dinga yi duk lokacin da ka tuno da shi my Angel " ya fada ya na kai hannu ya shafi geffen fuskar Vedad Daga kan shi sama Vedad ya yi ya na fadin " Daddy ! You know i really missed you everyday ,Allah ya jikan kan , ya yi maka rahama , Allah ya sa ka huta , kai da dukanin al'umar musulmi da su ka riga mu gidan gaskia , ina rokon Allah ya sa wannan adu'ar ta tarda ka duk inda ka ke , I love you my Superman " ya kai karshen ya na sakin wani kyawatencen murmushi A hankali Ash ya sa hannu ya janyo shi jikin shi ya rungume ya na fadin " na gwada maka wani abu ? " Da sauri Vedad ya dago da ga jikin Ash ya na fadin eh A hankali Ash ya koma ya jingina a jikin forehead din bed din shi sannan ya sa hannu ya dauki laptop din shi ya nuna wa Vedad geffen shi sannan ya shiga latsa laptop din Da sauri Vedad ya dawo geffen shi ya zauna ya na murmushi Ya na zama Ash ya mika mishi laptop din dai'dai wata video ta kama Wani kyawatencen murmushi Vedad ya saki lokacin da idanun shi su ka sauka kan abun da ke cikin videon Ba komai ba ne face Aylan shi da Vedad tun ya na karami ba zai wuce 3 years ba haka Su na zaune saman Lillo cikin Garden din nan na Gidan Aylan na farko Vedad sai tura fruits ya ke yi a baki Aylan na kallon shi ya na murmushi Su na a haka Kawai su ka jiyo Muryar Nihal ta na kwallawa Vedad kira Da sauri Aylan ya dauki Vedad ya bude jacket din shi ya saka shi a ciki sannan ya meda zip din kassa kassa ya ce " My angel yi shiru kar mummy ta jiyo ka , ta tafi da kai " Yar karamar dariya Vedad ya yi ya na cikin jacket din Aylan Dai'dai lokacin da Nihal ta karaso wajen lillon ta yi sallama sannan ta ce " Abban Ummi ina Vedad ya yi , tun safe na ke neman shi yaron na tsere ya buya " Cikin ko in kula Aylan ya ce " Duba wajen Khaled may be Ya na cen shi da Iqbal " Tsuke fuska Nihal ta yi ta ce " Abban Ummi minene ke motsi cikin jacket din ka " Yar karamar dariya Ummi da ke rike da wayar Aylan ta yi ta na toshe bakin ta Hararrar wassa Aylan ya yi mata kafin ya ce " Baby na ne , you don't know i'm Pregnant " Wata muguwar harara Nihal ta wurga ma Aylan , da sauri ya sa hannu ya zuge zip din jacket din shi Wani cool murmushi ta saki kafin ta koma geffen shi ta zauna ta daura hannun ta saman face din Vedad , har ya yi barci a jikin Aylan " Duba duk ya bata maka kaya " ta fada cikin sanyi Rungume Vedad tsam Aylan ya yi ya na fadin " ba komai" ya kai karshen ya na kai dan bakin shi ya sumbaci forehead din Vedad da ga haka videon ta kai end Yar karamar dariya Vedad ya yi ya dago kai ya kali Ash ya na mika mishi laptop din shi ya ce " big bro ina ka samo wannan videon ? " Ajiye laptop din saman bedside drawer Ash ya yi ya na fadin " a lokacin Ummi ta na rike da wayar Daddy ta na game , Ta cikin camera din na ga abun da ku ke yi , ai ni na fadawa mummy ku na garden " " you , you are wicked big bro " Vedad ya fada ya na kontawa ya rungume kugun Ash dan barci ya ke ji ya lumshe idanun shi Shi dai Ash bai ce mishi komai ba , sai a lokacin ya tuno da Iqbal da ke zaune saman sofa , duk abun nan da su ka yi bai ce uffan ba allamun ya yi barci ko akasin haka A hankali Ash ya kai hannu ya dauki pillow ya tila wa Iqbal A razane Iqbal ya dawo cikin hayacin shi Da sauri Ash ya ce mishi " Shut up !!!!!!!! Tunanin mi ka ke yi haka ? " Dan karamin tsaki Iqbal ya ja ya na kauda kai gefe ya na turo dan bakin shi ya ce " ni ba tunanin da na ke " " oya come here " Ba musu ya taso ya dawo dayan geffen shi ya zauna ya na ci gaba da turo dan bakin nan na shi " Fada min gaskia , ba dai wani abu ku ka yi kai da yarinyar nan ba " Ash ya tambaye shi , dan ya lura yadda sigar jikin shi duk ta ke mike Cikin ko in kula Iqbal ya ce mishi " ni fa ba abun da na yi mata , ai ita ta fara yi min kiss " " Kai kuma me ka yi mata ? " " Kiss kadai na yi mata , ni ban ma san ya a ka yi ba kawai sai jin hannun ta na yi , ta na kokarin saka shi cikin trouser di na " " ka bari ta saka ? " Da sauri ya girgiza mishi kai ya na fadin " no , ban bari ba " Okay kawai Ash ya ce kafin ya gyara konciyar shi , ya na rungume da Vedad Shi ma Iqbal konta wa ya yi su ka saka Ash a tsakiya " ka san wani abu ? " Iqbal ya fada ya na kallon Ash da ya lumshe idanun shi Girgiza mishi kai ya yi ba tare da ya bude idanun shi ba A hankali Iqbal ya matso ya kai bakin shi saitin kunen Ash kassa kassa ya rada mishi " Amma fa big bro , na ji dadin kiss din nan over " Cikin ko in kula Ash ya ce mishi " Okay bari in mu ka dawo da ga Nigeria , Sai ka yi abun da ya fi hakan ba wanda zai hana ka , but ka ce min Duk familyn ta a New York su ke zaune ko ? " " eh a NEW York su ke " " Tun yaushe ku ke tare da ita ? " " this year , wannan shekarar ce ta shigo university din mu , So za mu kai six to seven months haka " A hankali Ash ya gyada kan shi kafin ya ce " Kai ka ce ka na son ta " Yar karamar dariya Iqbal ya yi kafin ya ce " kai da ka san halin brother din ka , ita ta ce ta na so na , amma na ki yarda , Sai da ta matsa har kokarin kashe kan ta ta yi , sannan na hakura na yarda da ga baya na ji na kamu da son ta ni ma " Shiru Ash ya yi bai ce mishi komai ba " Tabass akwai wani abu a kassa " ya fada cikin zuciyar shi saboda Binciken da ya yi da safe bai samo komai ba a kan ta , ko university din su Iqbal da ya duba register din First year bai ga mai sunan Maya ba , hakan na nufin akwai wani abu a kassa may be aiko ta a ka yi dan cutar da familyn shi ? Ko ma minene ya dauki alwashin sai ya gano shi , dan ba zai bari wani abu ya sami brother din shi ba Da wannan tunanin har barci ya dauke shi , dan shi ma Iqbal ya jima da yin barcin shi * NIGER ( ZINDER STATE ) * KAUYEN NAWACH KALÉ ▪MISALIN KARFE 12 NA DARE * HAYAT 💦 A hankali ta sa kafa ta fito da ga cikin Dakin ta , ta na sanye da wata Gown duk ta kaude ta tsufa , ta na sanye da wannan hijabin ta na safe dama su biyu ne ta mallaka Hannu ta , ta na rike da wani kumshi na kaya cikin wani zane na atanfa Garin duk duhu ne , babu ko irin wanan tochilar a tsakiyar gidan , ba ka jin motsin komai sai kukan awaki da Shanu Amma a haka ta sa kafa ta fito dakin ta na tafiya cikin sanda kamar barawo , a haka ta nufi hanyar fita gidan , sai kale kale ta ke yi kar a je wani ya gan ta Har ta kai bakin kofar gidan ta jiyo Muryar inna ta na fadin " Waye a nan ? " ta fada ta na haska Hayat da torch din hannun ta Dum Hayat ta ji gaban ta ya fadi da sauri ta juyo ta kali inna , idanun ta na kawo ruwa ta shiga girgiza mata kai Ita ma inna tsaya wa ta yi ta na kare wa Hayat kallo ta kassa cewa komai Kamar da ga sama su ka jiyo Muryar wani mutun cikin dakin da inna ke tsaye bakin kofar shi ya na fadin " Barira wanene wai ? " Da sauri inna ta ce mishi " ba kowa Auwalu ne ya fito shan ruwa " ta na gama fadar haka ta juya ta shiga cikin dakin ba tare da ta ce wa Hayat komai ba Hayat na ganin ta shiga Dakin ta , ta sauke nanauyar ajiyar zuciya , ta juya da gudu ta fice gidan Ta na fitowa gidan ta daga rigar ta sama ta fara Gudu da wadanan kananan kafafun na ta , gudu ta ke cikin fitar hayaci , ko gaban ta ba ta gani , ga kuma garin duk duhu ne A haka kawai ta ji ta yi tuntunbe da wani dutse ta yi wata muguwar faduwa kassa dibb , amma ba ta tsaya duba in ta ji ciwo ko ba ta ji ciwo , ta tashi ta ci gaba da gudun ta , ita dai a yau ta kudurta sai ta bar kauyen nan , dan ba za ta iya auren rabeh ba , ta grimace ta mutu a kan ta aure shi Ta dauki wajen good 30 minutes ta na wannan gudun na fitar hayaci kafin ta fita kauyen ba ki daya , ba abun da ta ke gani sai ita ce , da ciyayi Duk da ta yi nisa sosai da kauyen , ba ta tsaya da gudun ta ba , babu alamun gajiya sam a tattare da ita Sannu sannu har ta share wajen good 1 hour ta na wannan gudun babu tsayawa , haka har ta wuce wani kasurgumin daji sannan ta fara Hango wani Haske a cen nesa da ita , allamun ta fara shigowa gari Ta na ganin hasken nan ta tsaya da gudun ta , ta na kallon gaban ta , ta saki wani kyawatencen murmushi ta na meda nunfashi Sai da nunfashin ta ya dawo dai'dai sannan ta ci gaba da gudun ta , ta karaso cikin garin Zinder Hanyar da ta biyo babu kowa sai lamps din da su ka haska wajen , ba ta dauki wani lokaci mai tsawo ba ta karaso Gidan Bus , dai'dai lokacin da motocin ke shirin tashi , a na ta saka kayan passengers a ciki Da sauri ta karaso wajen daya da ga cikin bus din geffen driver ta tsaya ta na fadin " Don Allah motar nan ina ta yi " Kare mata kallo da kyau driver din ya yi kafin ya ce " Nigeria ta yi , sai dai ta cika " Nan take wani kuka ya kubce mata , ita ba ta ma san ina ne Nigeria ba amma haka ta shiga rokon shi da Allah ta na fadin " Don Allah dan uwa ka yi hakuri ka saman min waje , wlh yan uwa na duk su na cen , mahaifi na ne ya rasu ina son na koma gida , don Allah , don son annabi , ka taimaka min " " shikenan shikenan ya isa haka , yanzu in ki isa Kano akwai wanda zai tarbe ki " ya fada dan har ga Allah ta ba shi tausayi Da sauri ta ce mishi " eh eh , akwai baban yaya na , da mu ka yi waya da shi a cen zai zo dauka ta " ta fada mishi Gyada kan shi ya yi a hankali kafin ya bude kofar shi ya sauko sannan ya ce mata ta hau Cike da murna ta Haye bus din , ta zauna geffen driver sannan ya Haye ya rufe kofar Ya kai hannu ya dauki gorar ruwa da ke gaban steering motar ya mika mata Da sauri ta sa hannu ta karba ta na yi mishi godiya kafin ta bude ta , ta baki babu ko bismillah ta fara sha , sai da ta shanye ruwan duka sannan ta sauko gorar ruwan ta na nishi godiya dama kishi ta ke ji Dan karamin murmushi ya yi kafin ya ce " me ye sunnan ki ? " " Shahd , amma Hayat a ke kira na da shi " " Masha Allah duka sunayan ma su dadi ne " Dan karamin murmushi ta yi ta na sunkuyar da kai kassa Shi ma dan karamin murmushi ya yi ya kauda kan shi gefe , da ga haka ba wanda ya sake cewa wani abu har lokacin tafiya ya yi , driver ya tada motar su ka kama hanyar Nigeria , su na barin gidan bus din ko kwana ya dauki Hayat ▪WASHE GARI Misalin karfe 8 na safe inna ta tashi da ga barcin ta , ta shiga dakin Hayat kamar ba ta san abun da ya faru ba ta fito da gudu ta na kara ta na fadin " Wayooo Allah na shiga uku , Hayat , Hayat , Adda Hayat ba ta cikin gidan " Da gudu mutuman da ta kira da Adda ya fito da ga cikin dakin shi babu ko riga a jikin shi ya na fadin " Barira me ki ke fada ne haka , duba da kyau ko ta shiga ban daki " Kukan kariya Barira ta saki ta na fadin " Adda na duba ko ina cikin gidan nan har bakin kofa na duba , babu Hayat har kayan ta babu su , Adda wlh guduwa ta yi , na shiga uku na ni Barira " " Barira na shiga uku , ina Shahd ta tafi , sati biyu saura auren ta da rabeh , ko na sayar da shanu na ba zan samu kudin biyan shi sadakin ta da ya bayar , ga shi kuma na kashe kudin , na shiga uku ni Issa " " Issa , ka na nufin dama Rabeh ya biya sadakin Hayat " Barira ta fada cike da rudu dan ita a iya sannin dala daya ba ta ga ni ba da sunnan sadakin Hayat " Eh ya biya , Jakka Dari ya ba ni kuma wlh na kashe su dan yanzu bai wuce , jakka ashirin su ka yi min saura ba " ya fada kamar zai yi kuka Daura hannayan ta saman kai Barira ta yi ta na fadin " Issa , Issa , Issa wlh ba za ka ga annabi ba , ka fi kowa sanin halin Rabeh cikin kauyen nan kuma a haka ka ce za ka dauki yarinya ta tilo ka aura mishi , ko dan ba kai ka haife ta ba , Issa wlh duk abun da ya samu yarinya ta , Allah ya isa tsakani na da kai " Rage sautin Muryar shi ya yi ya na matsowa kusa da ita ya na fadin " ke don Allah ki rage sautin Muryar ki , kar makauta su ji mu na shiga uku " Da sauri ta katse shi da cewa " sun yi dare in ba su ji mu ba , wlh Issa tun dare bai yi maka ba gwara ka fita nemo min yarinya ta , idan ba haka ba wlh zan dau kafa har birni na kai karar ka wajen yan sanda , macuci kawai , wlh na yi nadamar auren ka , kuma da ga nan gidan mu zan tafi ka kai min takarda ta na gaji da wannan auren azabar na ka " ta na gama fadar haka ta juya ta shigewar ta daki ta na kukan munafirci kamar ba ta san lokacin da Hayat ta bar gidan ba Nan ta bar shi sai faman muzurai ya ke yi , ya kali nan ya kali nan ya rasa abun da zai yi , ya na a haka Barira ta fito da ga cikin dakin ta , ta na yafe da wani gyale ta rike da wani buhu na kayan ta , ta tsuke fuska allamun ba wassa Issa na ganin ta ya nufe ta da sauri ya na fadin " Barira , Barira ina za ki je haka " Cak ta tsaya ta rike kugun ta , ta na fadin " ka sake ni , Issa , na gaji da auren ka , dama ko cen ba son shi na ke ba " Da sauri ya riko buhun kayan ta ya fadin " don Allah Barira ki tsaya ki ji mana , mu shawo kan matsalar nan tun kafin a jiyo mu " Bai gama rufe bakin shi ba , ta fido wata wuka da ga kugun ta , ta na fadin " Issa ka sake ni , ko na kashe ka " ( 🤣🤣🤣🤙🤙 wayoo Allah ciki na , Ku bawa Barira hannu don Allah ) Cike da tsoro Issa ya saki buhun ta , ya ja da baya , ya baya , Muryar shi har kerma ta ke ya na fadin " ke , ke Barira ba ki da hankali ne , ajiye wukar nan " Sakin buhun hannun ta ta yi ta sa hannu ta yaye kyalen ta , ta na daga murya ta ce " Eh ba ni da hankali Issa , wlh ka sake ni ko na kashe ka cikin gidan nan , ka kashe min miji na , ka raba ni da yarinya ta , yanzu kuma ka na son ka kashe ni ko , wlh sai ka sake ni ko ni na fara kashe ka " ta kai karshen ta na nufar shi da wukar Wata razananiyar kara ya saki kamar mace ya yi baya da gudu ya na fadin " ke lafiyar ki kuwa ko aljanai su ka shige ki " Da gudu ta nufe shi ta na fadin " eh aljanai ne , Issa ka sake ni , Ka sake ni ko na kashe ka , Yau ko mu ko kai cikin gidan nan yihuuuu , sai mun kashe ka Issa , Issa , Issa sai mun kashe ka " ta fada kamar mai aljanun gaske har wani nishi ta ke yi kamar mai farfadiya ta na biye da shi da gudu da wuka a hannun ta Shi kuma dan rashin hankali ya kassa shiga cikin daki kawai ya yi ta zagayen harabar gidan ya na kara ya na fadin " Jama'a taimako , Qul yaa ai-yuhaal kaafiruun , Quuluu aamannaa billahi wamaa unzila ilainaa wamaa unzila ila ibraahiima , bismillah rahim , A'uzubillahi mina sharrin Barira , Jama'a ku taimake ni za ta kashe ni " ya kai karshen kamar zai yi kuka Ya na gama fadar haka ya fada cikin dakin shi ya turo kofar ya danne da karfin shi , har wasu fitsari ya saki , yau ya ga mutuwa Duk da haka Barira ba ta kyale shi ba sai da ta bi shi ta na bugun kofar dakin da duk karfin ta ta na fadin " Issa ka sake ni , za mu kashe , za mu kashe ka " " Barira ki je na sake ki , don Allah ki kyale ni " " saki nawa " ta fada ta na barin bugun kofar " saki daya ! " ya fada Wani wawan bugu ta kai wa kofar da duk karfin ta , har sai da ya nemi faduwa ta na fadin " saki uku mu ke so " Cike da tsoro ya ce " ki je na sake ki saki uku " ya fada kamar zai yi kuka Ya na fadar haka Barira ta saki wani kyawatencen murmushi ta saki wukar hannun ta ta fado ta juya da sauri ta dauki buhun kayan ta , ta fice gidan ALLAH YA KARA MANA SON MANZON SA ❤ WAYOOO AMMA YAU NA SHA DARIYA 🤣🤣🤣🤙🤙🤙 TAURIN ZUCIYA 💖🌺💍 ( RETURN ) ( ROMANTIC LOVE STORY )💋🔥 ❤👑 MALLAKIN MEERAH 👑❤ اللَّهُمَّ صَلِّ عَلَى مُحَمَّدٍ وَعَلَى آلِ مُحَمَّدٍ، كَمَا صَلَّيْتَ عَلَى إِبْرَاهِيمَ وَعَلَى آلِ إِبْرَاهِيمَ، إِنَّكَ حَمِيدٌ مَجِيدٌ، اللَّهُمَّ بَارِكْ عَلَى مُحَمَّدٍ وَعَلَى آلِ مُحَمَّدٍ، كَمَا بَارَكْتَ عَلَى إِبْرَاهِيمَ وَعَلَى آلِ إِبْرَاهِيمَ، إِنَّكَ حَمِيدٌ مَجِيدٌ❤️ BISMILLAHIRRAHMANIRRAHIM PAGE 5 ❤🥂 TAღRIN ZღCIYA 💖🌺💍 ( RETღRN ) (ROMANTIC LUV STORY )💋🔥 ❤👑 ꪑꪖꪶꪶꪖƙỉ᭢ ꪖꪑꫀꫀꪹꪖꫝ ꪖꪉᦔꪮꪗꪶꪖꪗꫀ 👑❤ 𝗔.𝗞.𝗔 𝐀𝐍𝐈𝐒𝐇❥ 🕊💞 Wattpad : @bennybite Marubuciyar littafin TAURIN ZUCIYA EXILED PRINCE ( LOVE MEETS POWER ) TWO LIGHTS ( YAR JARIDA ) and now TAURIN ZUCIYA ( RETURN ) FOR MORE INFORMATION KU TABO WANNAN NUMBER +22798999753 WHATSAPP ONLY , Thanks 👍💕 اللَّهُمَّ صَلِّ عَلَى مُحَمَّدٍ وَعَلَى آلِ مُحَمَّدٍ، كَمَا صَلَّيْتَ عَلَى إِبْرَاهِيمَ وَعَلَى آلِ إِبْرَاهِيمَ، إِنَّكَ حَمِيدٌ مَجِيدٌ، اللَّهُمَّ بَارِكْ عَلَى مُحَمَّدٍ وَعَلَى آلِ مُحَمَّدٍ، كَمَا بَارَكْتَ عَلَى إِبْرَاهِيمَ وَعَلَى آلِ إِبْرَاهِيمَ، إِنَّكَ حَمِيدٌ مَجِيدٌ️ DOMIN SAMUN BOOK DI NA DA GA FARKO ZA KU IYA ADDING CHANEL DI NA TA WANNAN LINK 👇👇👇👇👇👇 https://whatsapp.com/channel/0029VaGhJCqKmCPUvpvIJ80i TAP THIS LINK TO JOIN MY WHATSAPP GROUP COMMETS SECTION 👇👇👇👇👇👇 https://chat.whatsapp.com/LWmuu0yv6C9DAhpdepDb4i 𝗧𝗔𝗣 𝗧𝗛𝗜𝗦 𝗟𝗜𝗞𝗘 𝗧𝗢 𝗝𝗢𝗜𝗡 𝗠𝗬 𝗣𝗢𝗦𝗧𝗜𝗡𝗚 𝗥𝗢𝗢𝗠 👇👇👇👇👇👇👇 https://chat.whatsapp.com/LepRstkGv3sDf8Jj4Gm054 _________________✦✦✦✦✦✦✦✦✦✦✦✦✦✦✦__________________ [ 🅿🅰🅶🅴̥ 5 ❤🔥 ] Ya na fadar haka Barira ta saki wani kyawatencen murmushi ta saki wukar hannun ta ta fado ta juya da sauri ta dauki buhun kayan ta , ta fice gidan Ya na jin ta yi shiru ya bude kofar ya dan soko kai ya leko ya ga ko ta nan Sai ya ga gida fayam babu kowa , ajiyar zuciya ya sauke har da lumshe idanun shi ya na fadin " Allah na gode maka , Allah na gode maka , gwara na zo na bar kauyen nan , tun kafin Rabeh bai isko ni ba , na san ta shi haukar ta fi ta Barira musaman a kan kudi " ya fada shi kadai kamar dani mahaukaci ya shiga tattare kayan shi da sauri sauri ya hada cikin dan buhu ya fice gidan da sauri Bangaran Barira kuma sai da ta yi nisa da gidan sannan ta tsaya ta bushe da wata shegiyar dariya , har da dafe ciki kamar mahaukaciya har da hawaye bibiyu Sai da ta yi dariyar ta iya son ran ta sannan ta yi shiru ta fara takawa a hankali cike da nitsuwa ta nufi hanyar gidan su ta na fadin " Haiiii barka Barira , yau tsawon shekara goma sha biyu Allah ya raba ki da Jarabbabe , shege matsiyaci kawai " ta na kai karshen ta sake bushewa da dariya a haka har ta isa gidan su ta na dariya kamar mahaukaciya Ita dama ta jima ta na son ta rabu da Issa amma ba hali , a daren jiya da ta ga Hayat na neman guduwa wani tunanin ya fado mata a rai , me zai hana ta yi anfani da wannan damar ta kirkiro wata masifar da zai sa Issa ya sake ta , shi ya sa ba ta yi kokarin tsayar da Hayat ba ta bar ta , ta yi tafiyar ta BARI MU LEKO MUTANAN US NA SAN KAFIN NAN BARIRA TA ISA GIDAN SU 🤣🤣🤣🤣🤙 ▪US ( WASHINGTON DC ) *MISALIN KARFE 2 NA DARE ▪ASH 🔥 A hankali ya ke tako stair din gidan ya sauko parlourn Kassa Har ya nufi dining room ya ga haske da ga cikin part din Nihal Ajiyar zuciya ya sauke kafin ya juya ya nufi part din Nihal , ya na isa ya tura kofar ya na sallama cen kassan makoshi Nan ya ga Nihal da Rayan su na zaune saman sofa three seaters A tare su ka kai kallon su wajen kofar su na amsa mishi sallamar shi sannan Rayan ya daura da cewa " General ba ka yi barci ba " Karasowa ya yi cikin parlourn ya zauna saman sofar geffen ta su ya na fadin " His excellency ba ka yi barci ba " Murmushi mai dan sauti Rayan ya yi kafin ya ce " ban yi ba , na zo yi wa sister di ta Allah kiyaye hanya , amma ban ji dadin rashin bin ku ba wlh , na so na je Nigeria ni ma ko dan na ga su Haidar " " Yaya Rayan , ka bari idan mun dawo sai ka tafi , ka ga Ash sai ya kula da office din shugaban kassa " Nihal ta fada ta na murmushi " mummy ni fa ba zan iya aiki shugaban kassa ba , ko shi his excellency da ya ya ke yi " Ash ya fada ya na kallon Rayan Yar dariya Rayan ya yi kafin ya ce " General , wlh aikin shugaban kassa babu sauki , ni har na fara nadamar hawa na wannan kujerar " " To sai a ci gaba da rikewa dan babu wanda zai hau ta cikin gidan nan " Ash ya fada ya na mikewa Da sauri Nihal ta taro shi ta na fadin " Ash ina za ka je haka " " zan koma na yi barci , dama My angel ne ya tada ni wai fruits zai sha " ya fada ya na sa kafa ya fice part din Da kallo su ka raka shi har sai da ya fita sannan Rayan ya juyo ya kali Nihal ya ce " Sister ya kamata mu kawo karshen gwaurancin General & Marshal , dubi ki ga yadda ya sangar ta Vedad , ki na fa ji cewa ya yi My angel , gaskiya ya kamata a nemo mishi mata " Yar dariya Nihal ta yi kafin ta ce " kar ka damu Yaya Rayan , kai dai ka roki Allah , ya hada ni da kyakyawar yarinya , mai tarbiya , da adini , wlh ko sun ki , ko sun so sai sun yi aure " Hararrar wassa Rayan ya yi mata ya na fadin " ke dai , ke dai sister yaushe ki ka koyi mugun ta haka " Dariya sosai Nihal ta yi kafin ta ce " yaya Rayan ba wata mugun ta , ai mu ma haka a ka yi mana kuma ga shi , yanzu har da yaran mu hudu , ka ga hakan shi ne hanya ma fi sauki da za mu aurar da su , in mu ka ce mu bi ta ra'ayin su wlh ba za su yi auren nan ba " " Gaskiya ki ka fada , amma sai mun yi a hankali " " kai dai yaya Rayan ka bar maganar nan a hannu na za ka sha mamaki " ta fada cikin gwarin guyiwa Dan karamin murmushi Rayan ya yi kafin ya ce " shikenan , ki dai kula min da kan ki sister Allah ya kiyaye hanya ya dawo min da ku lafiya , ya dawo da ku lafiya sister di na " Ita dai Nihal da amine ta ke amsa mishi da ga haka su ka yi sallama ya fice part din ya tafi na shi , ita kuma Nihal ta tashi ta shiga bedroom din ta ta wuce toilet ta yi wanka sannan ta shirya cikin kayan barcin ta , ta konta asuba ta gari ▪WASHE GARI Misalin karfe 8 dai'dai na safe duk mutanan gidan su ka shirya har da Rayan su ka fice gidan su ka kama hanyar international airport of Washington-Dulles Duk wasu shirye shirye da za a yi an riga da an yi su , Ash kadai a ke jira Airport din cike ya ke jibga jibgan sojoji da dankara dankaran motoci ma su nunfashi , ban ma yi kokarin kilga su ba dan na san ba zan iya ba wlh A haka su ka wuce kai tsaye cikin Jet din Ash , su na shiga ya daga ko , ya kama hanyar Nigeria , his excellency Rayan kuma ya kama hanyar white house kamar yadda su ka yi da Ash , sai dai mu ce Allah ya tsare ku , ya kai ku lafiya Bari mu leko su Hayat na san kafin nan jirgin su ya sauka ▪NIGERIA ( KANO STATE ) ▪HAYAT 💦 Misalin karfe 7 na safe bus din su ya shigo cikin garin Kano , Ta na tsaka da barcin ta mai mugun dadi driver ya tada ta , ya na ce mata ta tashi sun iso A rude ta tashi ta na bin wajen da kallo , ta na tambayar in sun iso " eh min iso , sai ki sauka ki tafi wajen dan uwan na ki , Allah ya kiyaye hanya " Driver ya fada mata Wasu yawu ta hadiye kafin ta ce mishi " dan Allah , dan uwa zan iya samun wani abu na ci wlh yunwa na ke ji " ta fada ta na marairaice fuska Dan karamin murmushi ya yi kafin ya kai ya dauki bread din da a ka sayo mishi da gorar ruwa guda ya mika mata Da sauri ta kai hannu ta karba ta na washe baki ta shiga jero mishi aduo'in godiya har sai da ya ce mata ta tafi ya isa haka Ba musu ta sauka da ga cikin motar , shi dai da kallo ya raka ta har sai da ta bacewa ganin shi sannan ya saki wani cool murmushi , har ga Allah yarinyar nan ta kon ta mishi a rai , ya ji tausayin ta sosai , sam yanayin idanun ta bai sa ya ji kyamar ta ba , sai ma burge shi da su ka yi , ya so ya raka ta har gidan su amma ba zai iya ba , dama saboda ita ya ba da kudi a ka amso mishi bread din nan , ko da ba ta tambaya ba , shi da kan shi zai ba , Sai dai na ce Allah ya biya ka , dan a wannan zamanin ba kowa ba zai yi irin wannan taimakon da ka yi ▪KADUNA ▪ KADUNA INTERNATIONAL AIRPORT Misalin karfe daya na yamma jirgin su Nihal ya sauka a cikin international airport na kaduna , allamun a kaduna za su sauka Airport din cike ya ke da manya manyan motoci ma su nufashi ma su bala'in kyau da tsada ni kassa kilga su ma na yi , ga ubanin sojoji cike da airport din kowane rike da gun , ba fa sojojin Nigeria , sojojin US ko shugaban kassar Nigeria da kan shi ba zai samu irin wannan tarbar ba , tun cikin daren jiya Rayan ya ba su umarni su taho , tare da wannan manyan motocin , musaman dan shirya zuwan familyn shi , har gidan da za su zauna sojojin nan sun riga da sun gyara komai Kai tsaye wajen motocin nan su ka nufa , Ash da junior su ka shiga mota guda , Ummi da Nihal su ka shiga mota guda , sai Iqbal da Vedad su ka shiga mota guda , a jere motocin su ka bar airport din nan da mugun gudu su na jiniya kamar wanda za su tashi sama Ba su dauki wani lokaci ba su ka iso cikin unguwar Nassarawa , Tun kafin su iso bakin kofar gidan , sojojin da ke cikin gidan su ka wangale musu kofar , su ka yi cikin gidan da mugun gudu Kai tsaye parking space su ka nufa , su ka yi parking din motocin su , sannan sojojin nan su ka fara dirowa da ga cikin motocin su da sauri sauri kawai ji ka ke dib dib dib Da gudu su ka nufi motocin mutanan gidan su ka bubude mu su kofa , su na sarawa Ash da junior Ash bai tsaya bin ta kan kowa ba ya daga kafa da sauri ya nufi cikin gidan Gidan ya na da girma sosai , Two floor ne sai wani dan balcony da ke hawa na biyun , an saka mishi wasu chair kamar na kaba , ma su mugun kyau Ya na shigowa parlourn ko tsaya wa bai yi ba ya nufi stair da sauri ya Haye abun shi Ya na hawa ko su Nihal su ka shigo cikin parlourn gidan , sai da su ka kare wa parlourn kallo da kyau sannan Nihal ta kale su ta ce " ku je ku dan huta " ta kai karshen ta na nufar wani corridor ta shiga part din kassa ita Ta na shiga junior, Iqbal da Vedad su ka Haye sama abin su , Ummi kuma ta bi bayan Nihal ta shiga part din da ke geffen na ta Kar ku tambaye ni ina kayan su , na ce muku tun daren jiya his excellency ya turo sojoji su ka gyara gidan , to tare da kayan su su ka taho , kowane su ka gyara mishi part din shi , shiga kawai za su yi Duk part 7 din bedroom biyu ne a ciki da parlour guda , part guda ke da bedroom daya sai parlour , shi ne kuma na Ash , wannan karan Iqbal da Vedad part guda su ka shiga , junior ma ya kama part din da ke kusa da na Ash ▪ASH 🔥 Bayan ya shiga part din shi , kai tsaye bedroom din ya wuce , ya na shiga ya wuce toilet dan ya yi wanka , ba su yi 30 minutes ba da shigowa Nigeria amma shi har ya fara jin zafin garin Sai da ya dauki wajen good one hour kafin ya fito da ga cikin toilet din daure da towel a kirjin shi Ya na shigowa bedroom din idanun shi su ka sauka kan Vedad ya na zaune tsakiyar bed din shi ya na rike da wayar shi ya na latsawa , ya na faman turo dan bakin nan na shi Ash bai bi ta kan shi ba ya wuce dressing room , jim kadan ya fito da ga shi sai short da singlet farare kal , ya saki wannan curly bakin gashin shi , sai tashin kamshi ya ke A hankali ya karaso bakin gadon ya zauna , ya kai hannu ya kwace wayar shi a hannun Vedad sannan ya ce " My angel tashi ka kawo min fruits " Noke kafada Vedad ya yi ya na kauda kai gefe Cikin nitsuwa Ash ya tambaye shi " me ya ke faruwa kuma ? " " Big bro wai me mu ka zo yi cikin garin nan mai mugun zafi , dubi tun dazu sai zufa na ke yi " ya fada cikin shagwaba Cikin ko in kula Ash ya ce mishi " mu je na yi maka wanka " " ni na yi wanka kafin na taho " " ka yi breakfast ? " " eh na yi " ya ba shi amsa a takaice Gyada kan shi Ash ya yi kafin ya ce " to minene matsalar ? " A hankali Vedad ya juyo kan shi ya na shirin magana Iqbal ya shigo bedroom din ya na sallama kassa kassa sai yamutse fuska ya ke yi Da Ash har Vedad duk kassan makoshi su ka amsa mishi sallamar shi Shi kuma ya na shigowa ya nufi bed din Ash ya Haye ya yi rub da ciki Mikewa tsaye Ash ya yi ya dauki laptop din shi da wayar shi , ya juya ya nufi wani glass da ke fuskantar door din shigowa bedroom din , Gadon na tsakiyar su Ya na isa kofar ta bude kan ta , ya daga kafa ya shiga dan balconyn , ya bar Iqbal da Vedad nan dan ya san in ya ce zai biye musu ba zai yi aikin da ya kawo shi ba Su kuma da kallo su ka raka shi har sai da ya shiga sannan Iqbal ya mike zaune ya na kallon Vedad ya ce " My Cutie pie , me ya faru na ga sai turo baki ka ke , ko dai big bro ya dake ka ? " Girgiza mishi kai Vedad ya yi kafin ya sauko da kafafun shi kassa ya mike tsaye ya mikawa Iqbal hannu ya na fadin " mu je ka raka ni wajen mummy " Hararrar shi Iqbal ya yi kafin ya ce " ba ka san hanya ba ne " Kukan shagwaba Vedad ya fara yi mishi har da bubuga kafafu a kassa ya na fadin " ni ban san inda ta ke ba " Mikewa tsaye shi Iqbal ya yi ya riko hannun shi ya na fadin " it's okay my Cutie pie , mu je ni ma wajen ta zan je " ya kai karshen ya na yin gaba Dan karamin murmushi Vedad ya yi ya na bin bayan Iqbal kamar rakumi da akala su ka fice part din baki daya Kai tsaye stair su ka sauko , su na shigowa parlourn su ka tardo Nihal da Ummi su na zaune Da sauri Vedad ya kwace hannun shi da ga cikin na Iqbal ya nufi Nihal da gudu ya fada jikin ta ya na fadin " mummy tashi mu koma gida ni ba zan zauna nan ba " ya fada cikin shagwaba dai'dai lokacin da Iqbal ya karaso cikin parlourn ya zauna geffen Ummi sannan ya ciro wayar shi da ga cikin trouser din shi ya shiga harkar gaban shi Nihal na shirin magana Ummi ta riga ta cewa " Vedad tashi da ga nan ko kunya ba ka ji ba , kai fa ba yaro ba ne " " ke kuma wa ya miki magana " ya fada ya na murguna ma ta baki Da sauri ta tasso ta na shirin bugun shi , da sauri Nihal ta tare ta ta na fadin " Ummi wlh ki kiyaye ni , me baby na ya yi miki da za ki buge shi " " mummy wlh duk ke ki ka ba ta wannan yaron , sai in ya yi wa mutun laifi ki ce ba za a taba shi ba " Ummi ta fada ta na komawa wajen ta ta zauna Yar karamar dariya Vedad ya yi ya na yi mata gwalo , abun ba karamar dariya ya ba ta ba ita da kan ta , ba ta san lokacin da ta yi mishi hararrar wassa ta na fadin " dube shi don Allah Big baby kawai " Yar karamar dariya ya yi kafin ya konta ya daura kan shi saman cinyar Nihal , sannan ya ce " Mummy , a cikin gidan nan ku ka zauna ke da Daddy ko ? " Girgiza mishi kai ta yi ta na daura hannun ta saman kan shi ba ce " no ba wannan ba ne , in ka na so zan kai ka " " eh mummy ina so , ina son na ga inda labarin soyayyar ku ya fara " Yar karamar dariya Ummi ta yi kafin ta ce " kai yanzu har ka san soyayya " " na sani mana , ga Iqbal nan ya na yi " A hankali Ummi ta juyo ta kali Iqbal , sai faman latsa wayar shi ya ke , ba ya ma tare da su Dawo da kallon ta ta yi kan Vedad ta na daga mishi gera guda ta ce " da wa ya ke soyayya ne ? " " ni ma ban sani ba , tambayi big bro " Mikewa tsaye Ummi ta yi ta nufi stair ta Haye Ta na hawa Vedad ya na dawo da kallon shi kan Nihal ya ce " mummy wai minene soyayya ? " Murmushi mai dan sauti Nihal ta yi kafin ta ce " My angel , ba ni da amsar da zan ba ka gaskiya , amma ka bari duk ranar da ka ji ka fada za ka san minene " " mummy ni fa babu inda zan fada " " haka shi ma Daddyn ka ya ce , amma duba ga ka nan zaune ka na zuba min shagwaba " ta kai karshen ta na ja mishi hanci " Kennan sai a na soyayya , a ke samun baby " " kai , Vedad tashi fice min da ga nan , so ka ke na fadi abun da ya fi karfin baki na , tashi ban waje " Ta na gama fadar haka ta ture kan shi , ta tashi ta shige corridor ta koma part din ta Dan karamin gunguni Vedad ya yi kafin ya tashi ya Haye stair ya koma part din shi Iqbal kuwa babu ma shi a wajen Allah kadai ya san abun da ya ke yi cikin wayar nan ▪ASH 🔥 Ya na zaune saman chair ya na aiki cikin laptop din shi kamar da ga sama ya ji ummi ta soko kai tsakanin shoulder din shi ta na fadin " kai ma soyayyar ce ka ke ? " ta kai karshen ta na janye kan ta , ta janyo chair ta zauna geffen shi Shi dai bai ce mata komai ba , ya ci gaba da aikin shi Dan karamin tsaki Ummi ta yi kafin ta kai ta kwace laptop din shi ta na fadin " ka ga dalilin da ya sa ba ni son yi maka magana, sai ka kyale mutun ni kuma ba ni son hakan " Slowly ya juyo da kan shi ya zuba mata wadanan sexy blue eyes din na shi ya ce " What happening ? " " nothing , kawai na zo na duba in kai ma ba ka fara soyayya ba ne " ta fada ta na duba laptop din shi , nan ta ga pics din yan mata dayawa a killa duk ba za su wuce 16 years ba , kuma da ga gani ba yan Turawa ba Dawo da kallon ta ta yi kan Ash cike da rudu ta ke fadin " Ash , wannan pics din na miye ? Ko matar auren ce ka ke nema haka " ta fada cikin zolaya ta na yar dariya Hannu ya sa ya karbi laptop din shi cikin ruwan sanyi ya ce mata " no , aikin da ya kawo ni ne nan " " kamar ban gane ba ? " Shiru ya yi na dan lokaci kafin ya mike ka mata laptop din shi , ba musu ta sa hannu ta karba ta na kallon screen din Da sauri ta lumshe idanun ta na kauda kai gefe ta na fadin " Inallillahi ! Minene wannan abun Ash ? " Karbar laptop din shi ya yi , kafin ya kashe ta , ya ajiye saman cinyar shi ba tare da ya ce komai ba A hankali Ummi ta bude idanun ta , ta juyo ta kale shi ta ce " Ba dai yaran nan ne ba " Cikin nitsuwa ya ce mata " su ne ? " " Oh my God , yanzu wanene zai yi wa yaran nan irin wannan abun , babu ko tausayi " " ni ma abun da na ke son sani kennan , shi ya sa na taho nan , a binciken da na yi , da ga Nigeria a ke kai yaran nan US da sunnan za a sama musu aiki " Cikin nitsuwa ta katse shi da cewa " da ga nan a yi sacrifices din su " A hankali ya girgiza mata kai kafin ya ce " no ba Sacrifice din su a ke yi ba " Shiru ta yi ba ta ce mishi komai ba dan ta ma rasa abun da za ce mishi A hankali ta kontar da kan ta saman shoulder din shi ta lumshe idanun ta , ta daura hannun ta saman na shi cikin sanyin murya ta ce " Ash kar a je su ne su ka kashe...... " Katse ta ya yi da cewa " no , ba su ba ne " " I really missed Him " ta fada kamar za ta yi kuka A hankali Ash ya lumshe idanun shi ya na bude su murya kassa kassa ya ce " Me too ! " Dan karamin murmushi Ummi ta saki kafin ta daura dayan hannun ta saman kirjin shi saitin zuciyar shi cike da zolaya ta ce " kenan wannan zuciyar ba ta dutse ba ce , Allah ya kawo wadda za ta shiga ciki to " Daura hannun shi ya yi saman na ta ya ce " bayan ke da mummy babu macen da za ta samu wuri a ciki " ya kai karshen ya na janye hannun ta Dago kan ta ta yi ta na kallon shi ta ce " kenan ka na so na , shi ne kuma ba ka taba fada min ba " ta kai karshen ta na marairaice fuska Slowly ya juyo ya kali face din ta " I love you more than my life " Wani kyawatencen murmushi ta saki kafin ta rungume shi ta na fadin " I love you too my little " A hankali ya zagayo da hannayan shi a bayan ta ya rungume ta shi ma , nan take ya ji wani sanyi cikin zuciyar shi , har ya manta last time da ya rungumi Twins din shi , amma ya san tun kafin ya fara horon soja ne , an jima gaskiya Dan bubuga mata baya ya yi ya na fadin " okay , sake ni na ci gaba da aiki na " Da to ta amsa mishi kafin ta sake shi , sai da ta manna mishi kiss a saman forehead din shi sannan ta tashi ta bar wajen , shi kuma ya dauki laptop din shi ya ci gaba da aikin shi ▪ZINDER ( KAUYEN NAWACH KALÉ ) ▪BARIRA Bakin ta dauke da sallama ta shigo cikin gidan na su Harabar gidan ta na da girma sosai , cen na hango wata mata zaune saman tabarma , dattijuwa ce gaskia , da ga gani za ta wuce shekara 60 Barira na ganin ta ta saki kukan munafirci , ta nufe ta gudu A rude matar nan ta ke fadin " Barira lafiya , me ya faru ki na kuka haka " ta fada dai'dai lokacin da Barira ta karaso ta zauna saman tabarma ta rungume matar nan ta na ci gaba da kukan ta , " kaka , Issa ya sake ni " ta fada cikin kukan na ta Cike da tashin hankali matar nan ke fadin " na shiga uku ya sake ki ? " Gyada mata kai Barira ta yi kafin ta daura da cewa " eh kaka , saki uku ma , kuma gashi ya sa Hayat ta bar gida kaka " " ban gane ba , kamar ya ta bar gida " A hankali Barira ta dago da ga jikin matar nan ta na fadin " eh kaka , kun fi kowa masaniya a kan auren da ya ke shirin yi mata da Rabeh , duka duka Hayat a nawa ta ke , ko al'ada ba ta fara ba , amma za ku sa ido ya dauke ta ya bawa mutumin da sai ya yi jika da ita , kaka Hayat ta tsere daren jiya , sai da ta ce min ita ba za ta aure shi ba amma na rufe ido , yanzu ga shi na rasa ta " " inallillahi wa'ina illaihi raji'un , yanzu ina Hayat za ta tafi " Matar nan ta fada kamar za ta yi kuka , Mikewa tsaye Barira ta yi ta nufi dakin da ke fuskantar su ta na ci gaba da kukan ta , kayan ta ma a nan ta bar su Ta na shiga matar nan ta mike ta nufi hanyar fita gidan ta fice sai sauri ta ke kamar za ta tashi sama , a haka har ta nufi fadar mai gari dan ta san wanda ta ke nema ya na cen Ta na karasowa fadar mai gari ta ga wajen cike da mutane , a rude ta karaso wajen ta na tambayar lafiya , ba ta gama rufe bakin ta ba idanun ta su ka sauka kan gawar Issa , gaban Mai gari , kan shi sai zubar da jini ya ke Ba ta san lokacin da ta saki wata razananiyar kara har da toshe bakin ta , nan take duk hankalin mutanan wajen ya dawo gare ta , da sauri wani dattijon da ke zaune kassa geffen mai gari ya taso ya nufe ta ya na tambayar me ya kawo ta nan Cike da rudu ta ke fadin " Malam lafiya me ya same shi ? " Bai ba ta amsar tambayar ta ba ya kamo hannun ta su ka juya ya na fadin " kontar da hankalin ki ba abun da ya faru , mu je gida zan fada miki " Ba musu ta bi bayan shi su ka koma gidan da ta fito , su na shiga ta shiga jero mishi tambayoyi Sakin hannun ta ya yi kafin ya juyo ya kale ta ya ce " komai ya wuce yanzu , Rabeh ne , ya tarda shi har gida ya yi mishi dukan tsiya wai ya cinye mishi kudin shi , yanzu haka maganar da na ke yi miki sun tafi su kai shi birni wajen yan sanda , shi kuma Issa a na jiran mai magani ya zo ya duba shi , abun da na ke so da ke , ki je gidan shi ki taho da Barira da Hayat tun kafin wani abu ya same su " " to ai Barira ta na cikin gidan nan " Ta fada mishi Cike da mamaki ya maimaita abun da ta fada Gyada mata kai ta yi kafin ta ce " eh , dalilin da ya sa ma na je fada neman ka , Hayat ta tsere ta bar garin nan , ita kuma Barira Issa ya sake ta , malam don Allah ka sa samarin garin nan su tafi neman ta tun wani abu bai same ta ba " ta kai karshen kamar za ta yi kuka Bayan inallillahi ba abun da malam ke fada , ya na dan zazaro idanu ya ma rasa abun da zai ce Duk maganar nan da su ka yi a kunnen Barira ta na jin su amma ta ki fitowa sai ma Allah kara da ta ke yi wa Rabeh da Issa Bari dai mu dan leko Hayat mu gani TAღRIN ZღCIYA 💖🌺💍 ( RETღRN ) (ROMANTIC LUV STORY )💋🔥 ❤👑 ꪑꪖꪶꪶꪖƙỉ᭢ ꪖꪑꫀꫀꪹꪖꫝ ꪖꪉᦔꪮꪗꪶꪖꪗꫀ 👑❤ 𝗔.𝗞.𝗔 𝐀𝐍𝐈𝐒𝐇❥ 🕊💞 Wattpad : @bennybite Marubuciyar littafin TAURIN ZUCIYA EXILED PRINCE ( LOVE MEETS POWER ) TWO LIGHTS ( YAR JARIDA ) and now TAURIN ZUCIYA ( RETURN ) FOR MORE INFORMATION KU TABO WANNAN NUMBER +22798999753 WHATSAPP ONLY , Thanks 👍💕 اللَّهُمَّ صَلِّ عَلَى مُحَمَّدٍ وَعَلَى آلِ مُحَمَّدٍ، كَمَا صَلَّيْتَ عَلَى إِبْرَاهِيمَ وَعَلَى آلِ إِبْرَاهِيمَ، إِنَّكَ حَمِيدٌ مَجِيدٌ، اللَّهُمَّ بَارِكْ عَلَى مُحَمَّدٍ وَعَلَى آلِ مُحَمَّدٍ، كَمَا بَارَكْتَ عَلَى إِبْرَاهِيمَ وَعَلَى آلِ إِبْرَاهِيمَ، إِنَّكَ حَمِيدٌ مَجِيدٌ️ TAP THIS LINK TO JOIN MY WHATSAPP GROUP COMMETS SECTION 👇👇👇👇👇👇 https://chat.whatsapp.com/BoRRwG9bqUFBt4djqzcNbb DOMIN SAMUN BOOK DI NA DA GA FARKO ZA KU IYA ADDING CHANEL DI NA TA WANNAN LINK 👇👇👇👇👇👇 https://whatsapp.com/channel/0029VaGhJCqKmCPUvpvIJ80i 𝗧𝗔𝗣 𝗧𝗛𝗜𝗦 𝗟𝗜𝗞𝗘 𝗧𝗢 𝗝𝗢𝗜𝗡 𝗠𝗬 𝗣𝗢𝗦𝗧𝗜𝗡𝗚 𝗥𝗢𝗢𝗠 👇👇👇👇👇👇👇 https://chat.whatsapp.com/LWmuu0yv6C9DAhpdepDb4i _________________✦✦✦✦✦✦✦✦✦✦✦✦✦✦✦__________________ [ 🅿🅰🅶🅴̥ 6 ❤🔥 ] ▪NIGERIA ( KANO STATE ) ▪HAYAT 💦 Bayan ta baro gidan Bus tafiya ta fara yi saman titi sam ba ta san inda za ta je ba , amma ita ko a jikin ta , sai ma tafiya ta ke ta na cin bread din ta , ta na korawa da ruwa Har sai da cinye kayan ta sannan ta fara lura da inda ta ke , Dum ta ji gaban ta ya fadi lokacin da idanun ta su ka yi mata arba da wata dankareriar mota da ta yo kan ta da mugun gudu A razane ta saki wata irin razananiyar kara ta na sakin kumshin kayan ta , ta na toshe kunnuwan da duka hanayan ta biyu ta lumshe idanun ta , ta na jiran motar nan ta buge ta , Amma sai ta ji shiru Slowly ta bude idanun ta , ta na kallon kassa sai ganin tayoyin motar nan ta yi dab da kafafun ta , A hankali ta dago kan ta , idanun ta ba su sauka ko ina ba sai saman wata kyakyawar mace , sanye cikin wani tsadaden lace milk colour ya na da ratsin baki , an yi mata babban dinki , ta yi daurin dan kwalin ta irin wannan no respect , ko gyale babu a jikin ta , ta yi uban make up , abun har ya ba ka tsoro amma ya yi mata kyau over , a shekaru za ta kai 40 haka , amma da ga ganin fatar jikin ta , ta na samun hutu irin wadanan manyan hajiyoyin A hankali ta dafa shoulder din Hayat ta na fadin " daughter ba ki ji ciwo ba dai ko ? " Gyada mata kai Hayat ta yi allamun a'a Kallon Hayat matar nan ta yi da ga sama har kassa , sannan idanun ta su ka sauka kan kumshin kayan ta , nan take ta saki wani kyawatencen murmushi , ta kai hannu ta dauko kumshin kayan ta , ta riko hannun ta ta na fadin " shikenan mu je na rage miki hanya " Ita dai Hayat da ido kawai ta ke bin ta , ta kassa cewa komai Haka matar nan ta bude kofar wajen mai zaman banza ta ce ma Hayat ta shiga , ba musu ta shiga sannan matar nan ta rufe kofar , ta bude gidan baya ta saka kayan ta , sannan ta ragayo ta shiga mazaunin driver ta tada motar su ka bar wajen Sai da su ka dan yi nisa sannan matar nan ta kali Hayat ta ce " ya sunan ki daughter " Wasu yawu Hayat ta hadiye kafin ta ce " Hayat " Gyada kan ta matar nan ta yi ta na dan tabe baki sannan ta ce " shikenan Hayat , ina zan sauke ki ? " ta fada ta na kallon ta ta wutsiyar ido Dan sunkuyar da kai Hayat ta yi ba tare da ta ce komai ba " a'a daughter lafiya , ba ki fada min ba , kar na wuce gidan na ku " matar nan ta fada cike da damuwa A hankali Hayat ta bude baki kamar za ta yi kuka ta ce " guduwa na yi da ga gidan mu , kuma ba zan koma ba " " asha , ki yi hakuri ki fada min ina ne gidan ku , saboda ba garin nan na ke ba , kaduna zan wuce , ba zan iya tafiya da ke ba " Nan take Hayat ta fashe da kuka ta na girgiza kai ta ce " don Allah ba zan koma gida ba , auren dole su ke son yi min , ni zan bi ki don Allah kar ki meda ni " " yanzu in su ka shiga neman ki , a ka gan ki tare da ki za qu ce sato ki na yi don Allah ki yi hakuri ki fada min , kar ki janyo min matsala " " babu wanda ya san na taho kuma , kuma ba da garin nan na ke ba , da ga Niger na ke , babu wanda ya san nan na taho " Parking motar ta matar nan ta yi geffen titi sannan ta juyo ta kali Hayat ta ce " shikenan , zan tafi da ke kaduna da sharadin bayan sati guda zan meyar da ke gidan ku " Da sauri Hayat ta gyada mata kai ta ce " eh eh na yarda " Dan karamin murmushi matar nan ta yi kafin ta zaro handkerchief guda ta mikawa Hayat ta ce ta goge hawayen ta , ba musu Hayat ta kai hannu ta karba ta fara goge hawayen ta Ta na karba matar nan ta juya ta tada motar ta su ka bar wajen ▪ KADUNA ▪ASH 🔥 Zaune ya ke cikin parlourn part din shi , da ga shi sai short da singlet , ya daure wanan lalawsan gashin kan shi a baya ya sako wasu dan sirarren a gaban goshi , sai baza kamshi ya ke yi , ya kurawa Tv gaban shi ido babu ko kiftawa Ya na a haka Iqbal ya shigo parlourn ya na sallama kassa , ya karaso geffen Ash ya zauna Ba tare da ya juyo ba Ash ya ce mishi " What's wrong with you , tun da safe na ga sai kai kawo ka ke yi " Dan karamin tsaki Iqbal ya yi kafin ya ce " Big bro , Wai me ya kawo mu Garin nan , ba mu yi ten hours ba da zuwa amma har na yi wanka shidda , saboda zafi " " and ? " ya fada a takaice " kamar ya and ? Ina fada maka zafi na ke ji ka ce min and , so ka ke sai na mutu " Iqbal ya fada kamar zai yi kuka " ni na san ba zafi ba ka ke ji , fada min gaskiya , ita ce ta fada maka ka dawo ko " Dan zaro idanu Iqbal ya yi , baki sake ya ke fadin " how did you know ? " " ka na kewar ta ne ? " Ash ya tambaye shi Dan kontar da kan shi ya yi saman shoulder din Ash ya ce " sosai ma , i don't know why duk lokacin da na rufe ido ina tuna........ " shiru ya yi ya kassa kai karshen maganar shi Slowly Ash ya juyo ya kale shi , da sauri Iqbal ya kauda kai gefe ya na musurai da idanu " why ka yi shiru ida maganar ka " Ash ya fada dan ya gane abun da ya ke son cewa Da sauri Iqbal ya tashi ya na shirin fita dakin , amma bai yi taku daya ba , Ash ya riko hannun shi cak ya janyo shi da karfi ya dawo ya zauna inda ya taso Cikin tsare gida Ash ya ce mishi " za ka kai karshen maganar ka , ko sai na fido shi da karfi " Kukan shagwaba Iqbal ya shiga yi mishi ya na fadin " uhmm uhmm , Ni fa ba abun da zan ce " " Shut up , ba na haka yi min wannan shirmen ba " kunbure fuska Iqbal ya yi ya na turo dan bakin nan na shi ya na shirin magana Ash ya riga shi cewa " Oya stanp up ka fara Frog jump " dan zaro idanu Iqbal ya yi ya na fadin " Frog jump ? no , Really big bro frog jump sai dai Vedad ni na girma " ya kai karshen ya na kauda kai gefe gyada kan shi Ash ya yi kafin ya ce " gaskiya ne , dole ka ce ka girma ka fara jin kamshin mace ba dole ba , za ka tashi ka fara ko sai na " dan karamin gunguni Iqbal ya yi kafin ya tashi , ya koma tsakiyar parlourn ya tsuguna ya fara frog jump , ya san duk lokacin da Ash bai kai karshen maganar shi ba to ba da wassa ya ke ba , yanzu in ya ce ba zai yi ba , wlh dukan tsiya zai yi mishi kuma ba me raba su gidan nan sai da ya dauki wajen good ten minutes ya na frop jump ko sannu Ash bai ce mishi ba su na a haka Vedad ya turo kofar Parlourn ya shigo ya na sallama ya na ganin Iqbal na frop jump ya bushe da wata shegiyar dariya , ya nufi sofar da Ash ke zaune ya zauna geffen shi ya na ci gaba da dariyar shi har da dafe ciki wata muguwar Hararra Iqbal ya wurga mishi cikin zuciyar shi ya na fadin " za mu hadu waje " kamar ko Ash ya san abun da ya fada cikin zuciyar shi sai ya ce mishi " Babu inda za ku hadu , ka na taba shi sai na yi maka dukan kawo ruwa " turo dan bakin shi Iqbal ya yi wai shi ya ji haushi a hankali ya mike tsaye ya na kallon Ash ba tare da ya ce komai ba daga mishi gera Ash ya yi allamun minene ? murguna mishi baki Iqbal ya yi kafin ya nufi hanyar fita parlourn da gudu a dubu dari Ash da Vedad su ka mike a tare su ka bi bayan shi da gudu Iqbal ya shige part din shi ya wuce bedroom , ya turo kofar ya na shirin rufe ta Ash ya damko ta da hannun shi , Vedad ya shigo cikin dakin ya rungumo shi ta baya ya na fadin " Big bro , ga shi na riko shi " sakin kofar Ash ya yi ya shigo bedroom din sannan ya tura kofar ta rufe kan ta sannan ya danna wani button a jikin ta , a hankali ya juyo ya bai ce ma Iqbal komai ba , ya nufi bed din shi ya dauko pillow guda biyu sannan ya dawo ya ce ma Vedad " sake shi " ya kai karshen ya na mika mishi pillow guda cike da mugun ta Vedad ya riko pillow su ka fara bugun Iqbal da shi bawan Allah sai kara ya ke ya na fadin su kyale shi , amma ina Vedad an samu mugun ta , shi dama Ash ina ruwan shi bai san ragowa ba ko kadan da gudu Iqbal ya nufi bed din shi su na biye da shi su na bugun shi ya dauki dayan pillow shi ba ya shiga ramawa , ya na yar dariya shi da Vedad Ash kuma ya na ganin su na dariya shi da Vedad ya daina bugun Iqbal ya koma saman bed din ya zauna ya na ci gaba da kallon su , su na wassan su kamar kananan yara sai da su ka yi mai isar su sannan su ka Haye saman bed din su ka konta su na ci gaba da dariyar su , har ga Allah Ash ba karamin dadi ya ke ji ba cikin zuciyar shi duk lokacin da ya gan su cikin wannan yanayin a hankali Ash ya mike ya nufi door ya danna wani button din da ya danna da farko , sannan ya bude kofar ya kai ya fice ya na fita Iqbal da Vedad su ka mike zaune , su ka kali juna " My Cutie pie , wai ka San abun da ke damun big bro ne , kwana biyu ya zama wani haka haka " Iqbal ya fada , dan ya lura wani abu ya sauya a tattare da dan uwan na shi daga mishi gera guda Vedad ya yi ya na fadin " kamar ya kenan , ni ban ga komai ba " hannu Iqbal ya kai ya dunguri kan Vedad ya na fadin " dama ya za a yi ka gane , bayan wassa ba abun da ke cikin wannan kan na ka " murguna mishi baki Vedad ya yi ya na hararrar shi kafin ya sauko da ga saman gadon ya nufi hanyar fita gidan ya fice ya koma na shi bedroom wai shi ya ji haushin maganar Iqbal da ido Iqbal ya raka shi har sai da ya fita sannan ya yi yar karamar dariya ya koma ya konta ya lumshe idanun shi ya saki wani cool murmushi har da cije lips din shi na kassa ▪NIHAL 🥀 zaune su ke cikin parlourn gidan ita da Ummi , su na kallon Tv amma da ga gani hankalin su ba ya kan Tv din slowly Nihal ta juyo ta kali Ummi cikin sanyin murya ta ce " Ummi wai yaushe za ki fitar da mijin aure ni fa...... " da sauri Ummi ta katse ta da cewa " mummyyyyy , za ki fara ko , ni fa na fada miki ba na sha'awar yin aure " " Ummi idan ba ki yi aure ba me ki ke son yi ? so ki ke kullum ki dinga jera kafada da ni , Mutuncin ɗiya mace ya na gidan mijin ta , why ba ki so , ba ki son ganin babys din ki ? " " ba na son kasancewa cikin irin halin da ki ke ciki a yanzu , kullum sai kin yi wa rasuwar Daddy kuka , your happyness is incomplete without him , ba na zan iya jure rashin mutumin da na fi so a rayuwa ta ba kamar ke , mummy i'm not strong like you , please ki daina yi min wannan maganar ba na so " Ummi ta fada da dan karfi kamar za ta yi kuka wani cool murmushi Nihal ta saki kafin ta taso da ga saman sofar ta , ta dawo geffen Ummi ta zauna cikin sanyin murya ta ce " na sani shi ma da za a ba shi dama da ya dawo gare mu zai dawo ko da ta rana guda ce , na san duk inda ya ke a yanzu ya na mutuwar kewar ummin shi , amma kin sani mutanan da mu ke so tsakani da Allah ba su mutuwa , kullum su na rayuwa a cikin zuciyoyin mu , kullum mu na tunanin su kuma mu na yi musu adu'a , Gaskiya ki ka fada ina kewar Daddyn ku , kuma har ga Allah Farin ciki na ba zai taba cika babu shi , amma ba ki san dalilin da ya sa na ke yin kuka ba duk lokacin da na tuna da shi " cikin nitsuwa Ummi ta katse ta da cewa " In har da gaske ya na raye cikin zuciyar ki , why kullum sai kin yi kuka ? " dan karamin murmushi Nihal ta yi kafin ta ce " ni fa ba dan ya tafi ya bar ni ba ne na ke yin kuka , kawai ina tuno labarin soyayyar mu ne " yar karamar dariya Ummi ta yi ta na fadin " His maid " yar karamar dariya ita ma Nihal ta yi ta kai hannu ta dan bugi Damtsen ta , ta na fadin " ni ki kira da Maid ? " " no mummy ni fa cewa na yi His maid " hararrar wassa Nihal ta yi mata kafin ta ce " Gaskiya ne da Farko kallon yar aikin shi ya ke min , ni kuma ina mishi kallon sadauki na , har yanzu ina tina haduwa ta ta farko da shi , kallo guda na yi mishi na ji babu wanda na ke so a duniyar nan sama da shi , hmmm shi kuma ya shiga yi min jan aji " a tare ita da Ummi su ka yi dariya cikin dariyar ta ta Ummi ta ce " da gaske Daddy jan aji ya yi miki ? ai mata a ka sani da jan aji " ta kai karshen ta na sake bushewa da dariya " hmmm , The General of American Army Staff guda ki ce ba zai yi jan aji ba , mutumin da bude baki ma ya yi min magana wuya ta ke yi mishi ko gaishe shi na yi ba ya amsawa , sai dai in na yi mishi laifi ya shiga sa ni frog jump , Daddyn ku fa sam ba ya da sakin fuska , ko papi da ya haife shi ba zai iya kallon cikin idanun shi ya fadi wata maganar ba , ko murmushi ba ya yi , sai ya zauna cikin waje shi bai muku magana ba kuma ba ku da izinin yin magana " " hai fa mummy , Daddy fa ya na murmushi , har da dariya ma " " eh ya na yi , amma bai taba yin su ba gaban mutanan gidan , bayan haihuwar Iqbal ne ya fara yin murmushi gaban yan gidan , ina tine first time da su His excellency su ka ga murmushin shi har party sai da su ka yi mishi ranar nan " " party ? just for a smile " " hmmm , murmushin daddyn ku karshe ne , ko namiji ne ya ga murmushin Daddyn ku wlh sai ya burge shi , ina kuma ga mata , har yanzu ban ga mai murmushi irin na Daddyn ku ba " " that's why you love him " Ummi ta fada ta na kashewa Nihal gera guda Girgiza mata kai Nihal ta yi kafin ta ce " ko ɗaya , lokacin da na kamu da son shi ban ga wannan murmushin ba , lokaci guda na kamu da son shi , kuma har yanzu son nan ya na cikin zuciya ta bai sauya ba , a duk lokacin da na kale ku , ke da brothers din ki , sai in ji kamar ya na a kusa da ni , musaman idan na kali Ash , yadda ki ka ga Ash haka daddyn ku ya ke , kamar an tsaga kara , sai dai fa ina ga Ash sai ya fi daddyn ku miskilanci " ta kai karshen ta na dariya ita da Ummi kamar da ga sama su ka jiyo a na yi musu gyaran murya da ga bayan su a tare Ummi da Nihal su ka zaro idanu , a razane su ka juya idanun su ba su sauka ko ina ba sai saman Ash da ke tsaye tsakiyar stair ya nade hanayan shi a kirji ya zuba musu wadanan sexy blue eyes din na shi a hankali ya daga ya fara sauko stair din ya karaso bayan sofar su ya tsaya ya ce " gulmar mutane ku ke yi ko ? " kallon kassan ido Nihal ta yi mishi kafin ta ce " kai kuma labe ka ke yi wa mutane " shiru ya yi bai ce komai ya na ci gaba da kallon su sai da ya ƙare musu kallo da kyau sannan ya daga kafa ya nufi kofar fita da kallo Nihal da Ummi su ka raka shi sai da ya fita sannan su ka bushe da dariya a tare sai da ta tsagaita dariyar ta sannan Nihal ta ce wa Ummi " please Ummi ki fitar da mijin aure " " mummy ni fa ba auren ne ba na so ba , har yanzu ban ga wanda ya yi min ba " gyada kan ta Nihal ta yi kafin ta ce " sannun ki , to yanzu a ka je wanda ya yi miki , ke ba ki yi mishi ba " " sai na hakura " ta fada a takaice dan girgiza kai Nihal tayi ta na fadin " Ummi rayuwa fa ba haka ta ke ba , ka yi aiki da abun da ka samu " cikin nitsuwa Ummi ta katse ta da cewa " mummyyyyy , ni ma nawa sadaukin na ke jira , I want to be with a man like my dad, a man who could sacrifice his life for me, a man who will cherish me and make me his priority, a man who will accept me as I am with all my qualities and my faults " murmushi mai dan sauti Nihal ta yi kafin ta ce " a takaice dai you just want the perfect man ? " " Daddy was perfect ? " gyada mata kai Nihal ta yi ta na fadin " yes ! but in his own way " Dan karamin murmushi Ummi ta yi ba tare da ta ce komai ba mikewa tsaye Nihal ta yi ta daura hannun ta saman kumatun Ummi ta na murmushi ta ce " no man is perfect my darling, it's you who will make sure that he becomes perfect as you wish " ta na gama fadar haka ta juya ta nufi corridor da kallo Ummi ta raka ta , ta na murmushi murya kassa kassa ta ce " I love you mummy " ▪ASH 🔥 Bayan ya fito Parlourn kai tsaye Boys quarter ya nufa ya na neman junior duk Sojojin wajen su na ganin shi su ka mike da sauri su na sara mishi , bai bi ta kan gaisuwar su ba ya ce " Where is Marshal ? " " Ya Fita sir " Felix ya fada cikin girmamawa " shi kaɗai ya fita ? " " Yes sir " Ya na jin hakan ya juya cikin konciyar hankali ya koma cikin gidan , Kai tsaye part din shi ya wuce , ya shiga bedroom din shi ya dauki laptop din shi sannan ya dawo parlour ya zauna ya fara latsawa Dan zaro wadanan sexy blue eyes din nan na shi ya yi cike da rudu ya ke fadin " How can it be possible " Kamar da ga sama ya jiyo muryar Junior ya na fadin " na jima ai da na dawo " A hamkali Ash ya lumshe idanun shi ya bude su , Kafin ya dago kai ya juya ya kali junior ya na tsaye bakin kofar Parlourn ya jingina a jikin door din ya nade hanayan shi a kirji ya na murmushi a hankali ya saki hannayan shi ya karaso cikin parlourn ya zauna geffen Ash ya na fadin " ni dama na san sai ka ce za ka yi tracking di na shi ya sa na kashe Tracker din " dan kashe idanun shi Ash ya yi kafin ya ce " Ina ka je ? " " nowhere , kawai na fita zagaye garin ne , amma na jima da na dawo da ga nan na wuce garden Felix bai ga dawowa ta ba ne " gyada kan shi Ash ya yi kafin ya ce " Okay , but ya kamata ka dinga sanar da ni idan za ka fita " " Ash i'm not a baby please " junior ya fada ya na kauda kai gefe " it's true , kar ka manta aiki ne ya kawo mu nan , Idan ka san ba za ka iya ba za ka iya komawa US " " ya isa haka Ash ni fa ba kannen ka ba ne da za ka tsaya ka na yi min magana yadda ka ga dama , na san aiki ya kawo mu , shikenan sai a ce ba ni da izinin fita " " Marshal Aylan jalaludeen don't forget i'm your general ka san abun da za ka fada min " Ash ya fada da dan karfi dan magaganun Junior sun fara bata mishi rai allamun yau junior ya sha Tabar nan da ya ke sha dama haka nan ta ke yi mishi duk ranar da ya sha ta sai Rayan ya shiga tsakanin su , Ga Ash dama da zuciya , in ya na cikin fushi bai san abun da yake ba , shi kuma junior ya fadi duk abun da ke cikin zuciyar shi kamar wanda ya sha giya , da ga baya kuma su dawo kamar ba a yi komai ba , shi ya sa Ash ya ke son ya daina shan ta amma ya ki , har company da su ke buga Tabar a US sai da Ash ya sa a ka rufe ta amma ya rasa inda junior ya ke samo ta mikewa junior ya yi , ya na fadin " Ni kuma Big brother din ka ne , Respect me , na gaji da wannan abun da ka ke min kawai dan ka fi matsayi " ya kai karshen ya na juyawa zai fice parlourn cak ya ji an damko hannun shi , a dubu dari ya juya ya ga Ash ya riko hannun shi , ya waro wadanan sexy blue eyes din shi kamar su fado , sun yi jazir dan bacin rai lips din shi har kerma su ke yi ya na fadin " Junior , be careful i don't like that " bige hannun shi junior ya yi da karfi ya na tsaki ya juya bai yi taku biyu ba , Ash ya riko hannun shi , ya juyo shi da karfi ya dunkule hannun shi ya kai mishi wani wawan bugu a fuska , har sai da bakin shi ya fashe nan take a dubu dari Junior ya dago kai ya yi kokarin Kai wa Ash bugu , sai dai bai same shi ba ya gauce , Dama training din da su ka samu ba daya ba , tun Ash na shekara goma Aylan ya fara ba shi training din Soja , shi kuma junior bayan ya shiga Army ne ya fara karbar training kun ga Duk yadda za a yi Ash ya fi shi kwarewa wajen iya fada riko hannun shi Ash ya yi ya daga sama ya kai mishi wani mugun bugu a ciki har sai da junior ya fice parlourn ya fado cikin corridor din , dama su na kusan door din duk da ya ji zafin bugun amma bai hakura ba sai da ya tashi da karfi ya nufi Ash Kafin ba ya karaso Ash ya daga kafa ya tura shi baya har sai da ya furzo jini da ga bakin shi dai'dai lokacin da Vedad ya fito da ga part din su ya na ganin halin da Junior ke ciki ya saki wata razananiyar kara ya nufe su da gudu ya riko Ash ya na fadin " Big bro calm down please you are going to kill him " ina sam Ash ba ya jin shi yau ya kai makura dama ya gaji da iskancin da junior ke yi wa Rayan bayan idon su , ga tabar da ya ke sha a matsayin shi na Soja Hannu daya Ash ya sa ya ture Vedad cen gefe ya fadi kassa har sai da ya saki kara , ya nufi Junior ya damko bayan keyar shi ya nufi Stair ya Tila shi dai'dai Iqbal ya fito da ga cikin part din shi dama karar da Vedad ya yi ce ta fido shi ya na ganin Ash ya tila Junior ta stair ya nufe shi da sauri ya riko hannun shi ya na fadin " ya isa haka Big bro please za ka kashe shi " a cen kassa kuma Junior na ida sauko stair Ummi da ke zaune a parlourn ta taso da sauri ta nufe shi , ta zube gaban shi ta talabo kan shi , sannan ta daga kai ta kali stair din , Ash na tsaye ya kurawa Junior idanu babu ko kiftawa , duk jijiyoyin jikin shi sun fito baro baro , idanun shi sun koma jazir har tsuma ya ke , ga Iqbal rike da hannun shi ya na rokon shi su tafi A hankali Ummi ta girgiza mishi kai allamun ya isa da sauri ya juya ya bar wajen ya nufi part din shi Iqbal na shirin bin bayan shi Ummi ta ce mishi " Iqbal kyale shi , zo taimaka wa junior ya koma bedroom din shi , na duba shi " gyada mata kai Iqbal ya yi kafin ya sauko stair din da sauri ya karaso geffen junior , su ka kama shi da Ummi su ka tada shi tsaye sannan su ka nufi stair su ka fara takawa da kyair su ka iso part din shi kai tsaye bedroom su ka wuce da shi , su ka kontar da shi saman bed , sannan Iqbal ya juya da sauri ya fice Part din ya na fita ita kuma ta bude box din bedside drawer ta fido A box ta fara duba Junior da ga nan ta yi mishi allurar barci sannan ta fito bedroom din ta fice part din bangaran Ash kuma har zai shiga part din shi idanun shi su ka sauka kan Vedad , ya yi irin zaman bokaye ya sunkuyar da kai ya na kuka kassa kassa kamar baby a hankali Ash ya lumshe idanun shi ya sake bude su a kan Vedad kafin ya mika mishi hannu ba tare da ya dago kan shi ba ya daura hannun shi saman na Ash sannan ya mike tsaye su ka shiga cikin part din , kai tsaye bedroom su ka wuce ya zaunar da Vedad saman bed din shi , sannan shi ma ya zauna gefe ya na fadin " If you cry , I ........ " bai kai karshen maganar shi Vedad ya saki kuka kamar karamin yaro ya na fadin " let me , ni ba na son ganin ka , kar ka sake yi min magana , dubi yadda ka tura ni sai da na ji ciwo , ni na bata da kai " ya kai karshen ya na mikewa tsaye zai bar wajen Iqbal ya shigo bedroom din babu ko sallama da sauri ya taro Vedad ya rungume shi , Shi kuma Vedad sai kuka ya ke da duk karfin shi kamar baby dan karamin tsaki Ash ya yi kafin ya mike tsaye ya nufi toilet dan shi a yanzu ba ya cikin yanayin da zai rarrashin Vedad ya na shiga toilet din Iqbal ya ja Vedad su ka bar gidan kai tsaye su ka fice part din , maimakon ya meda shi bedroom din shi sai ya sauko stair da shi su nufi part din Nihal dan ya san bayan Ash ba wanda ke iya rarrashin Vedad sai Nihal ko knocking bai yi ba ya tura kofar ya shiga ya na fadin " mummy ! mummy ! " bai kai ga kiran na ukun ba , Nihal ta fito da ga cikin bedroom din ta , Vedad na ganin ta ya rabu da Iqbal ya nufe ta da gudu ya fada jikin ta ya na fadin " mummy , Big bro is wicked , duka na ya yi " a hankali Nihal ta dago kai ta kali Iqbal irin kallon nan na karin bayani kamar ko ya sani sai ya ce mata " Big bro ne su ka yi fada da Marshal , shi ne ya yi kokarin tare Big bro sai ya ture shi ya fadi kassa " janyo Vedad ta yi su ka zauna saman sofa sannan ta sa hannu ta fara goge mishi hawayen shi ta na fadin " My angel please stop crying , ka san ba na son ganin ka cikin wannan halin " noke mata kafada ya yi ba tare da ya ce komai ba dan karamin murmushi Nihal ta yi kafin ta ce " Shikenan If you stop crying zan je na yi maka Pancakes " a hankali ya fara rage sautin kukan shi ya na turo dan bakin nan na shi ya ce mata " Da gaske ? " " da gaske My baby " ta fada ta na ci gaba da goge hawayen shi mikewa tsaye ya yi ya riko hannun ya na fadin " to tashi mu tafi , ni yanzu na ke so " mikewa tsaye ita ma ta yi ta na fadin " sai ka daina kuka sannan " da sauri ya hannayan duka biyu ya goge hawayen shi ya na fadin " na daina shikenan , mu tafi yanzu " " ba ka yi min murmushi ba " dan karamin murmushi ya yi ya na shagwabe fuska ya ce " uhm uhm mummy mu tafi don Allah " murmushi mai dan sauti Nihal ta yi kafin ta riko hannun shi ta na fadin su tafi , su ka fice parlourn Iqbal na biye da bayan su bayan sun fita kai tsaye Kitchen su ka wuce , nan su ka tardo duk Chefs din su da ke shirya musu abincin su na ganin Nihal duk su ka shiga sara mata su ka koma gefe su ka tsaya Vedad kuma kabar ba shi ne ba me kuka yanzu , sai ya nufi babban cikin su duka ya na fadin " Chefs ku tafi duk na sallame ku mummy na za ta yi min Pancakes yau " a hankali chef ya dago kai ya kali Nihal gyada mishi kai ta yi ta na fadin " Za ku iya tafiya idan mun gama sai ku dawo " a tare duk su ka sara mata sannan su ka nufi dayar hanyar fita kitchen din har ya kai bakin kofar ya jiyo Muryar Nihal ta na fadin " Chef ko za ka iya fidomin kayan ban san inda su ke ba " " yes madam " ya fada cikin girmamawa kafin ya dawo cikin kitchen din ya nufi wasu closet ya fido mata Flour , Milk , Vanilla , bakin powder , Sugar , chocolate , maple syrop , sannan ya nufi fridge ya fido mata eggs ya kawo komai saman yar Desk din tsakiya ya ajiye , sannan ya koma ya dauko basket din fruits ya ajiye , da Bowl da whisk sannan ya nufi wani closet ya ciro stewpan ya daura saman gas cooker da ga haka ya koma gefe ya na fadin " Ku na bukatar wani abu madam " " no shikenan , za ka iya tafiya nan da one hour sai ku dawo " Ta fada ta na nufar desk din da kayan ke sama jinjina mata kai ya yi kafin ya juya ya fice shi ma TAღRIN ZღCIYA 💖🌺💍 ( RETღRN ) (ROMANTIC LUV STORY )💋🔥 ❤👑 ꪑꪖꪶꪶꪖƙỉ᭢ ᩏꪹỉ᭢ᨶꫀకక ꪑꫀꫀꪹꪖꫝ 👑❤ 🕊💞 Wattpad : @bennybite Marubuciyar littafin TAURIN ZUCIYA EXILED PRINCE ( LOVE MEETS POWER ) TWO LIGHTS ( YAR JARIDA ) and now TAURIN ZUCIYA ( RETURN ) FOR MORE INFORMATION KU TABO WANNAN NUMBER +22798999753 WHATSAPP ONLY , Thanks 👍💕 اللَّهُمَّ صَلِّ عَلَى مُحَمَّدٍ وَعَلَى آلِ مُحَمَّدٍ، كَمَا صَلَّيْتَ عَلَى إِبْرَاهِيمَ وَعَلَى آلِ إِبْرَاهِيمَ، إِنَّكَ حَمِيدٌ مَجِيدٌ، اللَّهُمَّ بَارِكْ عَلَى مُحَمَّدٍ وَعَلَى آلِ مُحَمَّدٍ، كَمَا بَارَكْتَ عَلَى إِبْرَاهِيمَ وَعَلَى آلِ إِبْرَاهِيمَ، إِنَّكَ حَمِيدٌ مَجِيدٌ️ TAP THIS LINK TO JOIN MY WHATSAPP GROUP COMMETS SECTION 👇👇👇👇👇👇 https://chat.whatsapp.com/BoRRwG9bqUFBt4djqzcNbb DOMIN SAMUN BOOK DI NA DA GA FARKO ZA KU IYA ADDING CHANEL DI NA TA WANNAN LINK 👇👇👇👇👇👇 https://whatsapp.com/channel/0029VaGhJCqKmCPUvpvIJ80i 𝗧𝗔𝗣 𝗧𝗛𝗜𝗦 𝗟𝗜𝗞𝗘 𝗧𝗢 𝗝𝗢𝗜𝗡 𝗠𝗬 𝗣𝗢𝗦𝗧𝗜𝗡𝗚 𝗥𝗢𝗢𝗠 👇👇👇👇👇👇👇 https://chat.whatsapp.com/LWmuu0yv6C9DAhpdepDb4i _________________✦✦✦✦✦✦✦✦✦✦✦✦✦✦✦__________________ PAGE ............7 ..........❤🥂 bayan chef ya fita Nihal ta kali Iqbal ta ce " To kai malam da ka biyo mu sai ka dauki wuka ka fara yanke Fruits " ta na gama rufe bakin ta Vedad ya daura da cewa " yawwa mummy , ni kuma zan kale ku idan kin gama na taba na ji in ya yi " ya kai karshen ya na Hayewa saman desk din hannu Iqbal ya kai ya dunguri kan shi kafin ya nufi wajen da su ke ajiye knife ya dauko sannan ya dawo ya fara yankar fruits Nihal kuwa ta dauki bowl ta zuba flour , bakin powder , vanilla flavour ta juya sannan ta dauki wani bowl ta fasa eggs din a ciki , ta zuba two spoon ta Sugar ta juya sannan ta zuba milk din a ciki ta juya su ka shiga cikin juna , sannan ta Zube mixture din cikin ta flour ta juya da kyau sannan ta nufi gas cooker ta kunna sannan dauki wannan mixture din da ta hada ta koma gaban gas cooker ta ajiye ta fara zubawa cikin pan din kamar da ga sama ta ji an rungumota ta baya sai da ta dan firgita a hankali ya kontar da kan shi saman shoulder din ta ya na fadin " mummy dayawa fa za ki yi , sai na kai wa big bro " " sannu malam , ba yanzun nan ka ida cewa ba shi da kirki , kuma shi ne za ka kai mishi Pancakes din ka " Nihal ta fada ta na ci gaba da kula da Pancakes din da ke cikin pan din " ba shi da kirki amma ai ni ina da shi ya sa zan kai mishi , mummy kin san favorite dish na big bro , ni fa ban taba jin ya ce ya na son cin wani abu ba , ko wanda a ka ba shi ba ya cinye shi dika " " No gaskiya ban sani ba , bai taba fada min " " To na Daddy fa , Tun da kin ce su na kama , kenan Favorite dish din su ma zai zo daya " wani cool murmushi Nihal ta saki kafin ta ce " Ba zan iya fada maka favorite dish din shi ba , amma na san Daddyn ka ya kware wajen iya girki , ko ni ya fi iya wa " da sauri Iqbal da ke bayan su ya ce " mummy ni fa ban taba ganin Daddy ya na girki ba " " ni kadai ya san da wannan , amma ai kun sha cin abincin da ya girka da kan shi , ko First time din da Vedad ya ci Pancakes shi ya yi su , your father was an excellent chef , Har yanzu ni dai ban ga wanda ya iya girki kamar shi ba " ta kai karshen ta na sakin wani cool murmushi , maganar ta tuno mata First time da ta ci grikin shi , har yanzu ba ta mance taste din Kazar amarcin su da ya girka mata da kan shi ( ko mu ba mu mance ranar nan ba ko ya ? 🤣🤣🤣🤣🤣🤙🤙🤙 ) ta yi nisa cikin tunanin ta ta jiyo Muryar Vedad ya na fadin " mummy zai kone " a razane ta dawo cikin hayacin ta , ta cire Pancakes din da ga cikin pan din ta juye shi cikin wani plate sannan ta zuba wani ta na fadin " Don Allah kun cika ni da surutu , dubi car wannan ta kusa konewa " yar karamar dariya Iqbal da Vedad su ka yi a tare sannan Iqbal ya ajiye knife din hannun shi ya karaso a hankali ya kontar da kan shi saman dayan shoulder din Nihal cikin sanyin murya ya ce " mummy fadi gaskia mu ne mu ka dauke miki hankali ko dai tunanin Daddy ki ka shiga yi " murmushin geffen fuska ta yi ta na fadin " and so what ? ku ne ku ka hana ni yin tunanin shi cikin konciyar hankali mana " " mummy kenan ki na tunanin Daddy ? " Vedad ya fada " Sosai ma , Specially inda ya ke ce min ina yi mishi wayo " Nihal ta fada ta na yar karamar dariya " Ai Daddy gaskiya ya fada mummy ki na yi mishi waƴo " Vedad da Iqbal su ka fada a tare " oh haka nan ya ke fada muku ko " " Ehhhhhh " Vedad da Iqbal su ka fada a tare da dan karfi , dan ba kariya ta yi ba kullum sai Aylan ya ce musu ta na yi mishi wayo murmushi mai dan sauti Nihal ta yi ba tare da ce komai ba a haka ta ci gaba da aikin ta , Vedad da Iqbal su na konce saman shoulder din ta , har sai da su ta gama ta dauki plate din Pancakes din su ka koma wajen desk din tsakiya inda Iqbal ya ajiye fruits din da ya yanke , sannan ta ce kowa ya shirya na shi plate ita kuma ta ficewar ta a tare Iqbal da Vedad ko wane ya shirya plate din shi , sannan su ka bar kitchen din , shi Iqbal ya tsaya a parlour Vedad kuma ya Haye stair ya tafi part din Ash da sallama a bakin shi , ya shigo parlourn ya na rike da tray din da ya daura plate din Pancakes din a sama Ash kuma ya na zaune saman Sofa Three seaters , ya na sanye da wasu pajama farare kal ma su bala'in laushi , ya daure wanan curly hair din shi a baya sai tashin kamshi ya ke gaban shi Vedad ya karaso ya na ta sakin murmushi ya zauna kassan carpet ya ajiye tray din gaban shi ya na fadin " sauko mu ci , mummy ta gyara mana da kan ta " ya kai karshen ya na daukar Fork shiru Ash ya yi bai ce komai ba , kawai ya zuba mishi wadanan sexy blue eyes din na shi jin yadda ya yi shiru bai sauko ba ya sa Vedad dago kai a hankali ya kali Ash ya shagwabe fuska ya ce " ba za ka ci ba " girgiza mishi kai Ash ya yi slowly ya bude bakin shi murya cen kassan makoshi ya ce " no fara ina zuwa " da to Vedad ya amsa mishi kafin ya fara cin Pancakes din shi ya na murmushi kamar wani karamin yaro gwanin burgewa shi dai Ash haka ya tsaya ya zuba mishi wadanan sexy blue eyes din na shi , ya rasa dalilin da ya sa ya ke ji da Vedad sama da Iqbal , kamar gudan jinin shi haka Vedad ya ke wajen shi , ko dazu mistake ne a ka samu ya na cikin fushi ya ture shi ba dan haka ba , ko hannu mutun ya daura saman Vedad da sunnan cutar wa sai ya ga bayan shi ya yi nisa cikin tunanin shi kawai ya ga Vedad ya dago kai ya kale shi , bai ce mishi komai ba ya sakin mishi wani cool murmushi ya na fadin " big bro ni fa zan cinye duƙa " ya kai karshen cikin shagwaba " Okay cinye abun ka " Ash ya fada dan ya san dama da wuya ya raga mishi , Vedad ya na mugun son Pancakes ba zai iya yin kwana daya ba bai ci ba bai gama rufe bakin shi ba ya jiyo Muryar Iqbal ya na fadin " noooo , kar ka cinye raga min " ya kai karshen ya na karasowa cikin parlourn ya na rike da fork a hannun shi da sauri Vedad ya dauki plate din ya mike ya koma geffen Ash ya zauna ya na fadin " ba zan bayar ba , ai ni mummy ta gyara wa " marairaice fuska Iqbal ya yi ya na fadin " please my Cutie pie , wlh bai ishe ni ba " " ni dai ba zan bayar ba " ya kai karshen ya na kauda kai gefe a hankali Ash ya ce mishi " My angel ba shi mana " dan karamin gunguni Vedad ya yi kafin ya sauko kassa ya na fadin " zo ka ci , amma dan big bro ne ya ce na ba ka " dan karamin murmushi Iqbal ya yi kafin ya matso da face din shi ya kai dan bakin shi ya mannawa Vedad kiss a kumatu wani cool murmushi Vedad ya saki kafin ya sunkuyar da kan shi su ka ci gaba da cin Pancakes din a tare , Ash na saman sofa ya na kallon su gwanin burgewa ( ina ma Aylan na raye ya ga Triplets din shi cikin wannan farin cikin 😭😭😭💔💔 ) ▪HAYAT 💦 Misalin karfe 3 na yamma motar su ta shigo Garin kaduna wani ikon Allah kuma cikin unguwar da su Nihal su ka sauka , Hayat har ta yi barci cikin motar ta na tsaka da barcin ta ta jiyo Muryar matar nan ta na fadin " Daughter sauko mun iso " a razane Hayat ta farka ta na fadin " eh eh " yar karamar dariya matar nan ta yi ta na fadin " ke cewa na yi mun iso sauko " sai a lokacin da dawo cikin hayacin ta , ta sauko da ga cikin motar a hankali ta fara bin gidan da kallo gida ne mai girma gaskiya dai'dai mutun biyu da ga gani ita kadai ce cikin gidan nan dan ko ina a rufe ya ke " mu tafi ko " Matar nan ta fada ta na yin gaba da sauri Hayat ta bi bayan matar nan su ka nufi door din da za ta sada ka da parlourn gidan su na isowa matar nan ta bude bag din ta ta fido keys ta saka cikin kofar ta bude ta tura ta, ta na yin sallama wasu yawu Hayat ta hadiye kafin ta daga kafa ta bi bayan matar nan su ka shiga cikin parlourn , sai dai duk duhu ne cak ta tsaya waje guda zuciyar ta na duka uku uku ta na a haka ta ga wajen ya ɗauki haske har sai da ta dan lumshe idanun ta , ta na bude su a hankali parlourn ya na da dan Girma komai na cikin shi Milk colour ne , an kawata shi da wasu Royal sofa Milk colour ma su ratsin Gold sun yi bala'in kyau idan ka shigo a geffen dama akwai wata yar dining room me dauke da wata Dining table fara kal mai chair shidda, sai wata yar door a bayan su allamun ta kitchen ce geffen Dama kuma Stair ne da ga kassan shi akwai wasu door guda uku allamun bedroom ne ta yi nisa cikin tunanin ta , ta jiyo Muryar matar nan ta na fadin " Shigo ki zauna mana " ta kai karshen ta na nufar Dining room ta shiga kitchen fara bin wajen da kallo Hayat ta yi kafin ta tako a hankali ta karaso cikin parlourn ta zauna a kassa saman tiles ta na rungume da buhun kayan ta fitowa matar nan ta yi da ga dining room ta na rike da tray dauke da Glass biyu da gorar ruwa biyu ta dawo cikin parlourn ta ajiye saman table sannan ta zauna saman sofa three seaters ta na murmushi ta ce " haba daughter tashi ki hau sofa mana kin zauna a kassa " ba musu Hayat ta taso da ga wajen da ta ke , ta karaso wajen wata sofar maimakon ta zauna saman ta sai ta zauna a kassa murmushi mai dan sauti matar nan ta yi ba tare da ta ce komai ba , ta bude gorar ruwa guda ta zuba mata ruwan cikin glass din biyu sannan ta dauki gudan ta mikawa Hayat ta na yi mata bismillah girgiza mata kai Hayat ta yi ba tare da ta ce komai ba " kar ki ji tsoro ki saki jikin ki , kin ji ko ? " a hankali Hayat ta taso ta mika hannun ta ta karbi glass din ruwan ta koma inda ta taso ta na fadin " na gode " murmushi kadan matar nan ta yi ta na fadin " never mind , Na san za ki so ki san ko ni wacece " a hankali Hayat ta gyada mata kai allamun e dan jinkirtawa matar nan ta yi kafin ta ce " Suna na Hajiyah Basira , amma za ki iya kira na da Hajiyah , Ni kadai na ke zaune cikin gidan nan sai yaro na da ke zuwa a kai a kai , miji na ya rasu da jimawa , ina safarar kaya da ga kassashe daban daban , ko yanzu wani aiki ne ya kai ni Kano har na hadu da ke " shiru Hayat ta yi ba ta ce komai ita dai kallon matar nan kawai ta ke yi " Sha ruwan ki mana , da ga nan sai ki tashi ki shiga daki ki yi wanka ki cire kayan nan sai ki konta ki huta , kar ki damu mai aiki na ta na kan hanya an jima za ta zo " da to kawai ta Amsa mata sannan ta kai glass din hannun ta a baki ta sha ruwan kadan sannan ta tashi ta mayar da shi saman tray din mikewa tsaye matar nan ta yi ta na fadin " taso mu je ki yi wanka " ta kai karshen ta na juyawa da sauri Hayat ta mike ta dauki dan kumshin kayan ta , ta bi bayan matar nan su ka nufi daya da ga cikin door din kassan stair ta bude ta shiga ta na yi wa Hayat bismillah da sallama a bakin ta ta shigo dakin ta na bin shi da kallo daki ne dai'dai mutun daya , komai na cikin shi da ga white sai brown colours nuna mata wata door matar ta yi ta na fadin " shiga ga toilet nan ki yi wanka yanzu ina kawo miki kayan sakawa " ta na gama fadar haka ta juya ta fice bedroom din ta bar Hayat nan tsaye a hankali Hayat ta karaso cikin dakin ta ajiye kumshin kayan ta saman gadon sannan ta nufi toilet , ta shiga ta janyo kofar ta rufe tsaya wa kawai ta yi ta na bin wajen da kallo , cen ta hango wasu bucket biyu cike da ruwa kassan wani dan Fanfo a hankali ta fara cire kayan jikin ta , sannan ta nufi wadanan bucket din Bayan wasu mintina ta fito da ga cikin toilet din ta na daure da towel a kirjin ta , amma towel din ba wani mai girma ba ne , wadanan santala santalan cinyoyin na ta su na a waje gaskia ta wanku sai yau ta yi wankan kirki , har wani Haske ta kara , Color din skin din ta Chocolate ya fito paro paro gwanin burgewa ta na fitowa ta ga wata Gown Pink color saman bed din dakin da wani dan karamin hijab fari geffen ta a hankali ta karaso gaban gadon ta kai hannu ta dauki Gown din , nan ta ga pant da bra ajiye a kassan ta sai da ta ƙare wa gown din kallo da kyau sannan ya ajiye ta , ta dauki pant din nan da bra ta saka sannan ta saka Gown din , kamar an dai'dai ta da ita , ta zauna ma ta cip cip a jiki , breast din ta da hips din ta sun fito gwanin burgewa ta na shirin daukar hijab din Hajiyah ta shigo ta na sallama ta na rike da wani perfume a hankali Hayat ta dago kai ta na amsa mata sallamar ta kassa kassa cak matar nan ta tsaya ta na ƙare wa Hayat kallo cikin zuciyar ta ta na fadin " Masha Allah , Allahuma barik , Dole na gyara yarinyar nan ba kananan kudade zan samu a kan wannan kyawon na ta ba " wani cool murmushi ta yi kafin ta karaso cikin dakin ta na fadin " wacece wanan kuma ina Hayat ta yi " dan karamin murmushi Hayat ta yi ta na sunkuyar da kai wai ita ta ji kunya dariya sosai Hajiyah ta yi , sai da ta tsagaita dariyar ta sannan ta ce " wai kunya ta ki ka ji , Shikenan ga perfume ki Feshe jikin ki da shi , sannan ki fito ki ci abinci na san ki na jin yunwa " ta na gama fadar haka ta ajiye perfume din saman bedside drawer sannan ta juya ta fice ta na fita Hayat ta dauki karamin hijab din nan ta saka sannan ta dauki perfume ta feshe jikin ta da shi maimakon ta fita sai ta nufi dressing mirror a hankali , ta tsaya ta na kallon kan ta ba ta san lokacin da ta saki wani cool murmushi , ita da kan ta sai da ta ji ta burge kan ta ba karamin kyau ta yi ba , kamar ba yar Ƙauyen nan ba a hankali ta juyo ta nufi kofar dakin ta fice , ta fito parlourn nan ta isko Hajiyah zaune saman sofa ita da wani kyakyawan saurayi , kamanin su daya da Hajiyah sai dai ta fi shi haske saboda bliching karaso wa cikin parlourn Hayat ta yi ta na sallama cen kassan makoshi slowly saurayin nan ya dago kai ya na amsa mata sallamar ta a ra'rabe ita Hayat ba ta ma san ya na yi ba ta karaso cikin parlourn ta zauna saman carpet ta na sunkuyar da kai sai bin ta da kallo saurayin nan ya ke yi har sai da ta zauna sannan ya janye idanun shi ya kali Hajiyah ya ce " Hajiyah wacece wanan kuma ? " wani dan karamin murmushi Hajiyah ta yi ta na fadin " she's my guest yarinyar wata friend's di ta ce " gyada kan shi kadan sauran yin nan ya yi kafin ya kali Hayat ya ce " what's your name " ya fada da turanci shiru Hayat ta yi ba ta dago kan ta ba allamun ba ta ji abun da ya ce ba " ohhhh Ba ta jin turanci kai ma " ta fada dan ta san da wuya ne a ce ta na jin turanci dan ba ta yi kama da yaran da ke zuwa school ba kallon Hayat ta yi sannan ta ce " Hayat ! " a hankali Hayat ta dago kai ta na amsa mata da " na'am " nuna mata saurayin nan Hajiyah ta yi ta na fadin " Hayat wannan shi ne yaro na Razak , ki gaishe da yayan ki mana " gyada mata kai Hayat ta yi kafin ta juya ta kali Razak murya kassa kassa ta ce mishi " ina wuni ? " murmushi ya yi ya na fadin " lafiya lau , ya ki ke ? " " Lafiya " ta fada a takaice ta na sunkuyar da kan ta kallon Hajiyah ya yi cikin harshen turanci ya ce " Hajiyah ba za ki neman min auren ta ba gaskiya ta konta min a rai " hararrar wassa Hajiyah ta yi mishi ta na fadin " ba na son shirme da ga ganin yarinya sai ka ce ta kon ta ma ka a rai ? to tun wuri ka cire ta , nan gani nan bari " marairaice fuska ya yi ya na fadin " please Mum , why za ki yi min haka , ni gaskiya ina son ta " wani mugun kallo ta wurga mishi cikin zuciyar ta ta na fadin " ka ga dan iskan yaro ka na neman ka bata min shiri " cen kuma sai ta saki wani kyawatencen murmushi ta ce " shikenan zan yi magana da mamar ta , in ba a fitar mata da miji ba " wani kyawatencen murmushi Razak ya saki kafin ya ce " yawwa mummy na shi ya sa na ke mugun son ki " murmushi kadai Hajiyah ta yi ba tare da ce komai ba ita dai Hayat kamar babu ita a wajen , ga shi da turanci su ka yi maganar su ita kuma ba jin turanci ta ke yi ba su na a haka wata yarinya ta fito da ga cikin Kitchen ta na rike da wani tray dauke da wani plate rufe da wani plate din bakin ta da sallama ta shigo parlourn sai da Hajiyah ta amsa mata sallamar ta sannan ta ce " ajiye mata " ta kai karshen ta na nuna Hayat ba musu yarinyar nan ta ajiye tray din gaban Hayat sannan ta mike ta komawar ta kitchen ta na barin wajen Hajiyah ta ce ma Hayat " bude ki ci mana , na san ki na jin yunwa " gyada mata kai kawai Hayat ta yi kafin ta kai hannu ta bude plate din , ta sa hannu har za ta fara ci Hajiyah ta tsaida ta da cewa " a'a dauki spoon mana " a hankali Hayat ta gyada mata kai sannan ta kai hannu ta dauki spoon din da ke geffen plate din , a haka dai ta ka'kama duk da ba ta taba cin abincin da spoon ba amma sai da ta cinye jollof rice din nan tasss , sannan ta kora da ruwa , dama yunwa ta ke ji su dai Hajiyah da razak kallon ta kawai su ke yi su na murmushi har sai da ta gama sannan ta dauki tray din ta mike tsaye da sauri Hajiyah ta taro ta ta na fadin " zauna war ki , za ta dawo ta dauke shi " girgiza mata kai Hayat ta yi ta na fadin " zan kai mata " da to kawai Hajiyah ta amsa mata , da ga haka ta juya ta na rike da tray din ta nufi dining room bakin ta dauke da sallama ta shigo kitchen din nan ta isko yarinyar nan tsaye gaban gas cooker , slowly ta juyo ta na amsa mata sallamar ta " ina zan ajiye " Hayat ta fada cen kassa kassa wani desk yarinyar nan ta nuna mata ba tare da ta ce komai ba desk din Hayat ta nufa ta ajiye tray din sannan ta karaso geffen yarinyar nan ta tsaya ta na fadin " minene sunan ki ? " dan karamin murmushi yarinyar nan ta saki kafin ta ce " duk cikin yaran da Hajiyah ke kawowa gidan nan ke ce ta farko da ki ka yi min wannan tambayar , suna na Fatima " " kennan bayan ni akwai yaran da su ka sha zuwa gidan nan " Hayat ta fada cike da mamaki dan Hajiyah ta fada mata ita kadai ce a gidan bayan yaron ta ba me zuwa gyada mata kai Fatima ta yi ta na fadin " eh mana , ki na nufin ba aiki za ta samo miki ba " girgiza mata kai Hayat ta yi kafin ta ce " a'a kawai mun hadu da ita saman hanya shi ne ta kawo ni gidan ta " wani murmushi mai dan sauti Fatima ta yi kafin ta ce " ban cika shiga cikin harkar da ba tawa ba , amma da zan ba ki shawara tun wuri ki bar gidan nan , kafin ki yi nadamar shigowa cikin shi " cike da rudu Hayat ta tambaye ta " me ki ke nufi ? " dan karamin murmushin geffen fuska Fatima ta yi ba tare da ta ce komai ba ta ci gaba da aikin ta ita dai Hayat ta rasa me ta ke nufi da maganar ta , jin yadda ta yi shiru ba ta amsa mata ba kawai sai ta juya ta bar wajen ta fice kitchen din bayan ta fito kitchen din kai tsaye ta dawo parlour , har za ta wuce bedroom din ta , ta jiyo Muryar Razak ya na fadin " Sister ba za ki zo mu yi sallama ba , tafiya zan yi " cak ta tsaya ta juyo a hankali ta dawo cikin parlourn ta zuba mishi ido ta kassa cewa komai daga mata gera guda ya yi allamun minene girgiza mishi kai ta yi murya kassa kassa ta ce " Allah kiyaye hanya " ta na gama fadar haka ta juya da sauri sauri ta koma bedroom din da ta fito da ido ya raka ta har sai da ta shiga dakin ya na kallon bayan ta ,ya na lashe lips sai da ta shiga dakin sannan ya mike tsaye ya na fadin " Mum ni zan tafi may be nan da two days na dawo " mikewa tsaye ita ma Hajiyah ta yi ta na fadin " Okay , Allah ya kiyaye hanya Baby na , sai ka dawo " sai da ya kai bakin kofar sannan ya juyo a hankali ya ce " please mum kar ki manta magana ta " ya fada kamar zai yi kuka gyada mishi kai ta yi ta na fadin " shikenan Baby na , zan fada mata , sai ka dawo " ta na gama fadar haka ya sa kai ya fice gidan da kallo ta raka shi har sai da ya fita sannan ta ce " Gaskiya sai dai ka yi hakuri , amma ba zan aura maka yarinyar nan ba , akwai shiri na musaman da na yi a kan ta , wannan kyawon na ta ba kananan kudade zai kawo min ba " ta na gama fadar haka wayar ta da ke saman table , ta fara ringing hannu ta kai ta dauki wayar ta na kallon screen din wani kyawatencen murmushi ta saki kafin ta dauki kiran ta kai wayar a kunne ta na fadin " Alhajin Allah , yanzu ko na ke shirin kiran ka ! " shiru ta yi ta na sauraron abun da mutuman ke fada dan ni ba na iya jiyo abun da ya ke cewa shiru ta yi na dan lokaci kafin ta saki wata shegiyar dariya ta na fadin " Alhaji Alhaji , ban jima da dawowa ba , yanzu haka ina gida kai kadai ne ke jira , ka zo Aljihu cike dan na yi sabon kamu yau " yanzu ma dan jinkirtawa ta yi kafin ta ce " shikenan sai ka Zo Alhaji na " ta kai karshen ta na yar karamar dariya kafin ta sauke wayar da ga kunne ta katse kiran ta tashi ta Haye stair ▪ZINDER ( KAUYEN NAWACH KALE ) ▪BARIRA misalin karfe 8 na dare zaune su ke cikin harabar gidan saman tabbarma ita da Inna da malam , barira ta yi zugum idanun ta sun yi jawur duk sun kunbura saboda kukan da ta yi wani dogon nunfashi malam ya ja kafin ya ce " ki yi hakuri Barira , duk inda ta ke yanzu na san ta na hannun Allah , zai kula mana da ita , ya ƙare mana ita in sha Allah , Issa kuma Allah ya jikan shi ya yi mishi rahama " ya na gama fadar haka Barira ta saki wani sabon kukan ta na fadin " Sai da na fada muku , ba na son auren nan , ba al'hairi ba ne , amma kun ki ku ji , Issa da kan shi ya Kashe min mijina ya na dan uwan shi kuma , yanzu ya raba ni da yarinya ta tilo a duniya , mutuwa ba ta ishe shi ba , yanzu ina Hayat di ta ta shiga " dafa shoulder din inna ta yi cikin sigar rarrashi ta ce " don Allah ki daina kukan nan , in sha Allah za mu samo ta ba za ta wani nisa ba " MY BOOK IS ONLY ₦300 VIA 8081129487 Khadija Sabi'u Monie point bank KU TURA SHAIDAR BIYAN TA WANNAN NUMBER +22795577612 or +22798999753 اللَّهُمَّ صَلِّ عَلَى مُحَمَّدٍ وَعَلَى آلِ مُحَمَّدٍ، كَمَا صَلَّيْتَ عَلَى إِبْرَاهِيمَ وَعَلَى آلِ إِبْرَاهِيمَ، إِنَّكَ حَمِيدٌ مَجِيدٌ، اللَّهُمَّ بَارِكْ عَلَى مُحَمَّدٍ وَعَلَى آلِ مُحَمَّدٍ، كَمَا بَارَكْتَ عَلَى إِبْرَاهِيمَ وَعَلَى آلِ إِبْرَاهِيمَ، إِنَّكَ حَمِيدٌ مَجِيدٌ❤️ BISMILLAHIRRAHMANIRRAHIM FREE PAGE ............8.........❤🥂 cikin kukan na ta Barira ta ke fadin " Yanzu inna tsakani da Allah ba za mu tafi neman Hayat ba , wa ya san inda ta ke , hannun wa ta ke , wane hali ta ke ciki , ta ci abinci ko ba ta ci ba , Malam don Allah ni ku bar ni na tafi neman ta , wlh ba zan iya jure wa ba , hankali na ba zai konciya ba sai na gan ta " malam da ke zaune dayan geffen ta ya ce " Ki yi hakuri Barira , in sha Allah za mu samo ta , ba abun da zai same ta , ke dai ki kai kukan ki ga Allah ki roke shi ya tsare miki ita a duk inda ta ke , ba abun da zai same da da yardar Allah " a hankali barira ta fara rage sautin kukan ta , sannan ta ce " Shikenan malam , in sha Allah zan yi mata Adu'a Allah ya tsare min ita duk inda ta ke , ya medo ta gare ni " a tare Duk Su ka Amsa mata da Amine sannan inna ta sa hannu ta janyo Barira ta rungume ta sannu sannu har ta daina kukan da ta ke yi , ta fara sauke ajiyar zuciya a jere da ga haka ta tashi ta koma dakin ta , ta fara rokon Allah ya tsare ma ta Hayat duk inda ta ke , ya medo ta gida Lafiya , sannu sannu har karfe 12 na dare ya yi , ta na aduo'in ta a haka har barci ya dauke ta ba tare da sanin ta ba ▪KADUNA ( GIDAN SU NIHAL ) ▪ASH 🔥 konce ya ke saman katafaren gadon shi , da ga shi sai short da T-shirt , duk lamps din dakin a kashe su ke , sai wasu yan kananan bedside lamps a bayan gadon ma su launin blue mai mugun kyau dakin ya dauki wani mugun sanyi allamun sai da ya kai gudun ac karshe amma duk da haka jikin shi duk zufa ne kamar wanda a ka watsa ma ruwa , har wata yar kerma jikin shi ya ke yi ya na wata yar kara da lips din shi ya na girgiza kai a hankali , ga Dukan allamu ba lafiya a hankali Vedad ya turo kofar dakin ya shigo ya na rungume da pillow ya shagwabe fuska ko sallama bai yi ba ya ce " Big bro , na kassa barci , kuma , kuma ni yunwa na ke ji " ya kai karshen ya na zama bakin gadon jin yadda Ash ya yi shiru bai amsa mishi ba ya sa shi kai hannu ya kunna lamps din dakin ya na fadin " uhmm big bro da kai na ke ka kya....... " kut maganar ta yanke sakamakon idanun shi da su ka sauka kan Ash sai rawar jiki ya ke yi a rude Vedad ya saki pillown hannun shi ya Haye saman gadon baki daya ya kai hannu ya fara jijiga Ash ya na fadin " Big bro , lafiyar ka kuwa , Tashi don Allah bar min wannan wassan " shiru Ash ya yi ko motsi bai yi ba , sai rawar jiki ya ke yi kamar zai yi kuka Vedad ya shiga fadin " don Allah Big bro ka tashi , ka tashi ko na yi maka kuka " amma ina bayan rawar jiki ba abun da Ash ke yi da gudu Vedad ya sauka da ga saman gadon ya fice dakin da gudu ko ganin gaban shi ba ya yi kai tsaye part din Nihal ya wuce , tun da ga parlour ya ke fadin " mummy , mummy , where are you ? " ya kai karshen ya na shiga Bedroom din ta kai tsaye nan ya isko Nihal zaune saman daddumar ta , ta na sanye da wata Abaya Fara kal ta yi Rowling veil din ta sai tashin kamshi ta ke , ga kur'ani gaban ta , ta sunkuyar da kai ta na karantawa cikin nitsuwa a rude Vedad ya riko hannun ta ya na fadin " mummy taso mu tafi don Allah " dasa aya Nihal ta yi duk da ba ta kai karshen surar ba , ta dago kai ta ce " My angel lafiya ? me ya faru ne " kamar zai yi kuka ya ce " mummy please taso mu tafi ko gani , big bro ne tun dazu ina ta tada shi amma ya ki tashi " a dubu dari Nihal ta tashi , ta na rike da hannun Vedad su ka fice da sauri su ka Haye stair kai tsaye part din Ash su ka nufa su ka wuce bedroom din shi kai tsaye kamar an koro su haka su ka shigo cikin dakin idanun ta na sauka saman Ash gaban ta ya yi wata mumunar faduwa , sai rawar jiki ya ke yi , ga kuma wata uwar zufa da ya ke yi duk da ac da sauri ta nufi gadon ta Haye ta talabo kan shi ta daura saman cinyar ta , sannan ta janye bargon shi ta meda gefe ta na fadin " My little please open your eyes " shi dai Vedad ya na tsaye bakin gadon kamar ya yi kuka , bai taba ganin Ash cikin wannan halin ba ya na a haka Nihal ta dago kai ta kale shi ta ce " My angel kawo min ruwa " bai amsa mata ba ma ya juya da sauri ya fito parlourn ya nufi yar karamar fridge din da ke kusan Tv ya bude ya dauko gorar ruwa guda ya dawo cikin dakin da sauri ya mikawa Nihal karba ta yi ta bude ta , sannan ta zuba ruwa kadan a hannun ta , ta shafawa Ash a fuska a dubu dari ya ja wani dogon nunfashi ya na mikewa zaune , a rude ya kai hannu ya daga short din shi ya na kallon gaban shi , kafin ya diro da ga saman gadon da gudu ya shiga toilet ya turo kofar da karfi har sai da ta yi kara duk abun da ya ke Nihal da Vedad su na kallon shi amma ba su ce mishi komai ba sai da su ka ga ya shiga toilet sannan Vedad ya kali Nihal ya ce " mummy wai me ya samu Big bro " " My angel ni ma ban sani ba , tafi bedroom din ka ka yi barci na san kan shi ne ke yi mishi ciwo " noke mata kafadu ya yi ya na turo dan bakin shi ya ce " ni babu inda zan je ni da big bro zan kwana " " please my angel , ba ka ga ba shi da lafiya ba , shikenan tafi bedroom din na ga ni nan zuwa " dan karamin murmushi ya saki kafin ya juya ya fice part din ya nufi part din Nihal bangaran Ash kuma a rude ya shiga toilet din ya nufi Washbasin ya kunna fanfo ya tara hannun shi sannan ya watsa su a fuska , haka ya yi har so uku kafin ya dago ya kali cikin mirror din ya na nunfashi sama sama a hankali ya lumshe idanun shi ya na sauke wata nanauyar ajiyar zuciya , sannan ya bude slowly ya na ci gaba da kallon kan shi cikin glass din dan karamin tsaki ya ja kafin ya juya ya dauki Towel ya goge ruwan fuskar shi , sannan ya nufi door din fita ya fito Toilet din ya na shigowa bedroom din ya isko Nihal zaune bakin gado ta na jiran shi kallon ta ya ke cike da mamaki dan shi bai san cewa ta cikin dakin ba , karasowa ya yi bakin gadon ya na fadin " mummy what are you doing here a wannan lokacin ? " ya kai karshen ya na zama geffen ta ba ta ce mishi komai ba ta daura hannun ta saman forehead din shi ta na fadin " Little ba ka da lafiya ne ba za ka iya fada min ba , yanzu in wani ya same ka fa " " mummy i'm fine , ni fa ba na ciwon komai " matse gera ta yi ta na fadin " Okay , ba ka ciwon komai me ya sa jikin ka ya dau zafi , taba ka ji kamar wanda ke Fever " kauda kan shi gefe ya yi ya na fadin " mummy please i'm fine , go and sleep it's late " ya kai karshen ya na ida Hayewa bed din ya konta ya juya mata baya ya na bargo ya rufe jikin shi har zuwa kugu sannan ya lumshe idanun shi dan karamin murmushi Nihal ta yi kafin ta mike tsaye , ta kale shi ba dan mintina sannan ta sunkuyar da kan ta , ta manna mishi kiss a kumatu sannan ta ce " I love you my little " da ga nan ta kashe mishi wutar dakin ta fita ta jawo mishi kafar ya na jin duk abun da ta yi mishi har sai da ya fita sannan ya juyo kan shi a hankali ya kali kofar dakin sannan ya ce " I love you mummy " ya fada cen kassan makoshi da ga haka ya juya ya sake lumshe idanun shi ba jimawa barci ya dauke shi bangaran Nihal kuwa ta na fitowa part din shi kai tsaye na ta ta nufa bakin ta da sallama ta shigo bedroom din ta , nan ta isko Vedad ya yi ɗaye ɗaya saman bed din ta , ya lumshe idanun shi amma ba barci ya ke ba dan karamin murmushi ta saki kafin ta karaso cikin dakin ta zauna bakin gadon sannan ta lumshe idanun ta ta na zama ta ji vedad ya rungumota ta baya ya kontar da kan shi saman shoulder din ta ya ce " mummy wai me ya samu big bro ne , kin ga yadda ya tashi kamar wanda ya ga wani mugun abu " ba tare da ta bude idanun ta ba ta ce " My angel ina ga big bro din ka aure ya ke so na yi mishi " yar karamar dariya Vedad ya yi kafin ya ce " mummy shi da kan shi ya fada miki haka " girgiza mishi kai ta yi a hankali kafin ta ce " bai fada ba amma ni na san abun da ke cikin zuciyar shi , ko kai ma ka na son na yi maka auren ne " da sauri ya ce " no mummy ni ba ni so , i'm still a baby ban kai aure ba , ko big bro bai kai aure ba " yar karamar dariya Nihal ta yi ita maganar shi ta ba ta dariya wai shi har yanzu baby ne , santalelen saurayi kamar Vedad zai ce wai shi bai isa aure ba sai da ta gama dariyar ta sannan ta ce " Shikenan my baby , ba ka kai aure ba , amma dai Big bro din ka sai na yi mishi , kar a samu matsala da ga baya " " wace irin matsala kuma mummy " girgiza mishi kai ta yi ta na fadin " babu komai konta ka yi barcin ka , ni ma barcin na ke ji " da to ya amsa mata kafin ya kai dan bakin nan na shi ya yi mata kiss a kumatu sannan ya sake ta ya koma ya konta ya juya mata baya sai sakin murmushi ya ke yi a hankali ta saki wani cool murmushi ta na kallon shi har sai da ya konta sannan ta kai hannu ta kashe lamps din dakin , sannan ta ida Hayewa bed din ta konta , ta fuskantar ceiling ba tare da ta rufe idanun ta ba cikin zuciyar ta kuma ta na tunanin ina za ta samo yarinyar da za ta aurawa Ash , dan yanayin da ta ga ya Farka ya na duba cikin short din shi bai konta mata ba , may be shi ya manta amma ita ta tine ya taba yin hakan , first time da ya yi hakan tun ya na da shekara 13 lokacin da ya fara puberty , ya kamata ta samo mishi mata dan da ga gani irin wannan mafarkin ne ya yi da irin wannan tunanin ne har barci ya dauke ta ▪HAYAT 💦 misalin karfe 12 na dare , ta na tsaka da barcin ta , ta jiyo kamar wata yar kara dama ba wani nauyin barci gare ta ba , nan take ta farka da ga barcin ta a hankali ta fara ware idanun ta , ta na dan jujuya kan ta , ta kallon ceiling ta na a haka kawai ta sake jiyo wata karar a razane ta mike zaune ta na fadin " inallillahi , da ga ina wannan karar " da ga haka ta sauko da kafafun ta kassa ta mike tsaye , ta na murza idanun ta da hannu guda kafin ta yi wata doguwar mika ta na karanto kalmar shahada , a hankali ta daga kafa ta nufi kofar fita dakin ta na fitowa idanun ta su ka yi mata arba da wani mugun abu , nan take ta ji zuciyar ta yi wata muguwar bugawa , ta na zaro idanu da sauri ta kai hannu ta toshe bakin ta , dan ta na shirin sakin kara , ta koma cikin dakin da ta fito da gudu , ta turo kofar a hankali ta rufe ta koma bakin gado ta zauna ta na fadin " inallillahi wa'ina illaihi raji'un , inallillahi wa'ina illaihi raji'un , inallillahi wa'ina illaihi raji'un , ya Allah ka rabu da mugun gani da mugun ji , na shiga uku yau ni Shahd " ba komai ba ne ta gani ba sai Hajiyah ita da wani Mutun naked tsirara haihuwar uwar su , su na masha'ar su , kennan karar nan da ta jiyo ta Hajiyah ce a hankali ta saki wani marayan kukan , ta koma ta konta ta bawa kofar shigowa baya kenan Fatima ta san abun da Hajiyah ke yi shi ya sa ta ce mata ta bar gidan tun lokaci bai kure mata ba , Tirƙashi ta na a haka kawai ta ji an turo kofar dakin a hankali da sauri ta shanye kukan ta , ta lumshe idanun ta , zuciyar ta na duka uku uku ta na a haka ta jiyo Muryar Hajiyah ta na fadin " ka gan ta dai , ɗanya ce jaƙaf , ina ko period ma ba ta fara ba , Hope dai za ka kara wani abu saman wanda a ka saba " wata shegiyar dariya mutumin nan ya yi da wata Muryar shi babu dadin ji sam ya ce " Ai kar ki damu wannan karan ba kananan kudade za ki samu ba , da ga gani wannan yarinyar za ta yi ruwa " " hmmm Alhaji ba dai abun da na ke tunani ba ka ke shirin yi " wata yar karamar dariya mutumin nan ya yi kafin ya zagayo da hannu shi a kugun Hajiyah ta na kashe mata gera guda ya ce " na ma isa , ai bayan ke duniyar nan ban ga wadda ta kai sa wannan abun tashi bare yar karamar yarinya haka " yar karamar dariya Hajiyah ta yi ta na fadin " yanzu yaushe za ku zo daukar ta , tun ba ta ce za ta koma gidan su ba " " Kar ki damu nan da jibi zan turo yaro na , kadai kamin ban ki shiriya min ita da kyau " " ai ba sai na shirya ta ba , bari kai dai gobe za ka gan ta ba karamar kyakyawa ba ce " " shikenan Allah ya kai mu , yanzu dai wuce mu tafi dan ni fa har yanzu a hannu na ke " wata yar iskar dariya Hajiyah ta yi kafin ta juya ta fice dakin ta na tafiya kamar hawainiya , shi kuma sai da ya tsaya ya kali Hayat da kyau sannan ya bi bayan Hajiyah ya fice dakin su ka janyo mata kofar su ka ɗaura da ga inda su ka tsaya duk maganar da su ka yi a kunnen Hayat , dan ta na jin su sai da ta ji sun ja mata kofa sannan ta saki wani sabon kukan ta na sa hannun ta guda ta toshe bakin ta , hawaye na zubo mata bibiyu sai da ta yi kukan mai isar ta sannan ta tashi a hankali ta shiga toilet , ta wanke fuskar ta , sannan ta ɗauro da Alwalla , ta fito ta nufi wajen carpet din bakin gadon dan ba ta ga dadduma ba , ta fara Sallat ta na yi hawaye bibiyu na zubo mata , Haka ta Kamala nafilar ta , ta kai kukan ta ga Allah a kan ya fitar da ita da ga cikin gidan nan , ita ta gwanma ce auren Rabeh da wannan abun da idanun ta su ka yi mata arba da shi indai irin wannan abun ne Fatima ta ke yi mata magana a kai to tabass dole ta bar gidan a fitowar rana bayan ta Kamala Sallar ta , ta tashi ta koma bakin gado ta yi zaune ta na ci gaba da kukan ta kassa kassa cen kuma sai ta dago kai cike da kwarin guyiwa ta kai hannu ta goge hawayen ta , murya kassa kassa ta ce " a'a Shahd , kuka ba na ki ba ne , dole ki bar gidan nan tun lokaci bai ƙure miki ba , in har za ki iya tserewa auren Rabeh wadanan azzaluman ma za ki iya tsere musu " mikewa tsaye ta yi ta rike kugun ta da duka hannayan ta biyu ta na fadin " ba ke macuciya ba , za ki aiki na , yar iska mazinaciya kawai , annabi a baki , fir'auna a zuciya , wlh Shahd ta fi karfin zama yar iska irin ki , nan gani nan bari wlh na sha tabara na sha lahaula , na sha maganin matsiya ta ma su bakar zuciya , Ni ce nan jikar barbushi , aljannai ma sun gan ni sun kyale bare mutun " ta na gama fadar haka ta saki wata wata yar siririyar dariya , ta na kallon kofar dakin ta kassan ido ( mu dai mu na jira mu gani abun da zai faru ) ▪WASHE GARI ( Misalin karfe 8 ) ▪ASH 🔥 a hankali ya bude idanun shi , ba su sauka ko ina ba sai cikin na Vedad , ya na zaune geffen shi ya leko da kan shi ya na kallon face din Ash ya na murmushi a hankali Ash ya dago Hannu ya dan mari Face din shi cikin wata zazzakar murya cike da nitsuwa ya ce mishi " what are you doing here early ? " yar karamar dariya Vedad ya yi ya na janye kan shi ya na fadin " Big bro it's late not early , karfe 8 fa har da mintina " a dubu dari Ash ya mike zaune , ya kai hannu ya dauki wayar shi saman bedside drawer , ya kunna ya duba screen din , nan ya ga karfe 8 da mintina 26 meda wayar ya yi ya jingina bayan shi a jikin forehead din gadon sannan ya lumshe idanun shi a haka ya juya murya Vedad ya na fadin " Big bro , da wani abu cikin Duvet din ka " a hankali ya bude idanun shi ya kali Vedad ya daga mishi gera guda allamun minene cikin ko in kula ya kai dan yatsar shi saman Dick din Ash ya na fadin " wannan abun " ba Shiri Ash ya zaro idanun shi , sannu bai ce ba Vedad ba ya tashi a dubu dari ya nufi toilet da gudu , ya rufo kofar da karfi ya na shiga ya jingina bayan shi a jikin kofar ya na sauke ajiyar zuciya , a hankali ya dan sunkuyar da kan shi ya kali gaban shi , kafin ya meda kan shi jikin kofar ya na fadin " wai me ya ke shirin faruwa da ni haka , Just for a dream ? " ya na gama fadar haka ya nufi jacuzzi din shi ya tsunduma a cikin ko kayan jikin shi bai cire ba Vedad kuma ya na ganin Ash ya shiga toilet , sai ya dauki wayar shi ya shiga latsawa dan mintina , sannan ya tashi abin shi ya fice part din ▪NIHAL 🥀 zaune ta ke saman Sofa , ta na rike da wayar ta , ta na latsa wa cikin konciyar hankali ta na a haka kawai ta jiyo Muryar Vedad ya na kwalla mata kira a hankali ta dago kai ta kali saitin stair , nan ta gan shi , ya na sauko stair din da tsale kamar karamin yaro ita dai ba ta ce mishi komai ba har ya karasa sauko stair din , ya karaso cikin parlourn ya nufi sofar da Nihal ke zaune ya zauna geffen ta dan karamin murmushi ta yi kafin ta ce " wa kuma ya taba min Angel di na , ko ba ka yi breakfast ba " girgiza mata kai ya yi cikin shagwaba ya ce " no na yi breakfast , big bro ne sai yanzu ya tashi da ga barcin shi , ki cewa chef su shirya mishi na shi breakfast " " Ash sai yanzu ya tashi " ta maimaita kassa kassa , a iya sannin ta ko da su ke US , kiran Asubahi na farko da Ash a ke yin shi , ko ya Kamala sallar ba ya komawa barci , sai dai ya shiga Gym motsa jiki har sai karfe 7 ta yi , yau kuma ya tashi har 9 ba dan mintina , gaskiya akwai wata a ƙassa a hankali ta mike tsaye ta na ce ma Vedad ya jira ta ta na zuwa da ga haka ta Haye stair kai tsaye part din Ash ta nufa ta wuce kai bedroom din shi bakin ta da sallama ta shigo bedroom din dai'dai lokacin da Ash ya bude kofar toilet ya fito daure da towel a kugunshi ya na rike da wani karamin a hannun shi cen kassan makoshi ya amsa mata sallamar ta sannan ya nufi dressing mirror ya tsaya ya ba ta baya a hankali ta karaso ta tsaya tsakiyar dakin ta ce " Little wai me ya ke damun ka ne , Yanzu Vedad ke ce min wai yanzu ka tashi da ga barci , ko ba ka da lafiya ne " ba tare da ya juyo ba ya ce " i'm fine mummy " ya na gama fadar haka ya ji saukar hannun ta saman shoulder din shi , a hankali ya dago kai ya kale ta , ta cikin mirror hannun shi ta kamo ta jawo shi , ta zaunar da shi bakin gadon shi sannan ta zauna geffen shi , shi dai da ido kawai ya ke bin ta marairaice fuska ta yi kamar karamar yarinya ta ce " Alyasat ni fa na haife ka , na san akwai wani abun da ba ka son fada min , tun ka na karami ba ka taba boye min abun da ke damun ka ba sai yanzu , ko ka na tunanin yanzu ka yi girman da ba za ka iya fadamin ba ? " a hankali ya dan lumshe idanun shi kamar mai jin barci ya sake bude su a kan ta murya cen kassan makoshi ya ce " please mummy ki fahimce ni mana , na ce miki ba komai " mikewa tsaye ta yi ta na fadin " shikenan kar ka fadi , Ni kuma na yi maka alkawari ba zan saka komai a baki na ko ruwa ba zan sha ba , har sai ka fada min abun da ke damun ka " ta na gama fadar haka ta fara takawa za ta bar wajen a fusace da sauri Ash ya riko hannun ta , ya na fadin " please mummy kar ki min haka " juyo wa ta yi ta kale shi cikin tsare gida ta ce " little , ni fa mahaifiyar ka ce , Idan ba ka fada min damuwar ka wa za ka fadawa " sakin hannun ta ya yi a hankali ya sunkuyar da kai ya na fadin " ko na fada miki ba za ki gane ba ne " a hankali ta dawo geffen shi ta zauna ta na dafa shoulder din shi ta ce " just Tell me , i will understand you " a hankali ya sauke ajiyar zuciya ba tare da ya dago kai ba , murya cen kassan makoshi kamar ba ya son maganar ya ce " I don't know how it happened you know I never had these kinds of desire , I raped a girl and she died , I couldn't control myself I killed her mom, I arrested Rapists more than a hundred times and today I myself raped a girl who didn't even reach 15 years old and she died because of me " ya kai karshen ya na sunkuyar da kai Dum Nihal ta ji zuciyar ta ta buga a dubu dari ta mike tsaye ta na fadin " inallillahi wa'ina illaihi raji'un , Alyasat ta ya za ka yi irin wannan abun , na shiga uku yau ni Nihal , amma Alyasat ba ka rike amanar aikin ka ba , ka san ka na sha'awar mace ba za ka iya fada min ba na samu yarinya na aura maka , shi ne za ka je ka kashe ɗiyar mutane , ka cuce ni Alyasat , Yanzu fada min ina gawar ta ta ke " " yo ai mummy ke ki ka tashe ni kafin na San yadda zan yi da gawar ta " cike da rudu Nihal ta ce " ban gane abun da ka ke cewa ba " kauda kan shi dayan geffen ya yi ya na fadin " ina tsaka da mafarkin ki ka zuba min ruwa a fuska na tashi " nan take Nihal ta yi sumar tsaye lips din ta har kerma su ke yi ta bude ta ce " mafarki ? " a hankali ya gyada mata kai kafin ya ce " yeah a dream " " Ash , ba dai cikin mafarkin ka ba ka yi wannan abun da ka fada min " a hankali ya dago kai ya kale ta ya ce " it's just a dream mummy , ke fa ki ka ce na fada miki abun da ke damu na , sai da na ce miki baza ki gane ba , Hope dai ba tunanin ki ke ba hakan ta faru da gaske ? " nan take Nihal ta zube kassa ta yi irin zaman bokaye ta daura hannayan ta duka biyu saman kai kamar za ta yi kuka ta ce " Wayoooooo ni Allah , Abban Ummi ina ka shiga yau Alyasat zai sa zuciya ta ta buga " MY BOOK IS ONLY ₦300 VIA 8081129487 Khadija Sabi'u Monie point bank KU TURA SHAIDAR BIYAN TA WANNAN NUMBER +22795577612 or +22798999753 اللَّهُمَّ صَلِّ عَلَى مُحَمَّدٍ وَعَلَى آلِ مُحَمَّدٍ، كَمَا صَلَّيْتَ عَلَى إِبْرَاهِيمَ وَعَلَى آلِ إِبْرَاهِيمَ، إِنَّكَ حَمِيدٌ مَجِيدٌ، اللَّهُمَّ بَارِكْ عَلَى مُحَمَّدٍ وَعَلَى آلِ مُحَمَّدٍ، كَمَا بَارَكْتَ عَلَى إِبْرَاهِيمَ وَعَلَى آلِ إِبْرَاهِيمَ، إِنَّكَ حَمِيدٌ مَجِيدٌ❤️ BISMILLAHIRRAHMANIRRAHIM FREE PAGE ............9.........❤🥂 cikin konciyar hankali Ash ya ce mata " mummy ke fa ki ka ce na fada miki abun da ke damu na " mikewa tsaye Nihal ta yi ta nufi hanyar fita dakin ta na fadin " Wlh Ash ka ci uwar raina min hankali sama da Vedad ma , amma bar ka , zai yi maganin ka " ta na gama fadar haka ta fice dakin Da kallo ya raka ta har sai da ta fice dakin sannan ya tashi a hankali ya shige dressing room Nihal kuwa kai tsaye parlourn kassa ta sauko , nan ta isko Vedad da Iqbal su na zaune abin su Vedad na ganin Nihal ya tashi da sauri ya nufe ta ya na fadin " mummy mu tafi shan ice cream please , tun da mu ka zo har yanzu ba mu fita ba , kuma ni ina son mu fita na ga gidan da ku ka zaune ka da Daddy " ya kai karshen cikin shagwaba dan karamin murmushi ta yi kafin ta ce " shikenan je ka cewa Felix ya shirya za mu fita " ba ta gama rufe bakin ta ba ya juya da gudu ya fice parlourn , a hankali shi ma Iqbal ya mike ya bi bayan shi , dan ya gaji da zama cikin gidan su na fita Nihal ta ci gaba da takawar ta , ta nufi corridor ta shiga part din ta ba ta yi five minutes ba ta fito rike da wata yar bag , da face mask ta fice parlourn ta na fitowa sai saman wata dankareriar mota fara kal mai mugun kyau an yi parking din ta dai'dai kofar shigowa parlourn , Iqbal na mazaunin driver , Vedad na geffen shi dan karamin murmushi ta saki kafin ta karaso wajen motar ta shiga gidan baya ta na fadin " Ba tare da Felix za mu tafi ba ? " tada motar Iqbal ya yi su ka bar wajen ya na fadin " no mummy , ni na ce ya yi zaman shi " da okay kawai Nihal ta amsa mishi , da ga haka ya danna hanci motar waje ya na tambayar Nihal ina za su yi , nan ta ke ce mishi ya yi dama , ba musu ya yi dama su ka bar wajen ▪ASH 🔥 bayan ya Fitar Nihal da ga Bedroom din ya tashi ya shiga dressing room jim kadan ya fito sanye da Trouser black color da T-shirt white color , ya daure wanan curly hair din na shi a baya , Kafafun shi babu takalmi a ciki sai tashin fitinannan kamshi yake yi ya na fitowa ya nufi bed din shi ya zauna ya dauki laptop din shi ya shiga aikin shi bai yi five minutes ba da Zama Ummi ta shigo ta na sallama kassa kassa , ta sanye da kayan barcin ta , Duk gashin ta a tirje ya ke , da allamun ko wanka ba ta yi ba ba tare da ya dago kan shi ba ya amsa mata sallamar ta cen kassan makoshi a hankali ta karaso geffen shi ta zauna sannan ta yi baya ta konta a hankali ya bude bakin shi ya ce " What's wrong ? " wani dogon nunfashi ta yi kafin ta ce " nothing ! " ta fada a takaice da ya ke ya san yar uwar ta shi , ya san ba karamin abu ba zai kawo ta wajen shi tun da safe haka ko wanka ba ta yi ba a hankali ya ajiye laptop din shi saman bedside drawer , ya juyo kai a hankali ya kale ta ya ce " Oya stand Up , tell me what's wrong with you ? " dan karamin gunguni ta yi kafin ta mike zaune ta na sunkuyar da kai ta ce " ta ya ka san da akwai wani abu ? " dan jinkirtawa ya yi kafin ya ce " don't forget you are my twins , Idan wani abu na damun ki , ina iya jin shi a jiki na " dan karamin murmushi ta yi ta na fadin " It's true , ka na iya jin abun da ke damu na , ni ma ina iya jin abun da ke damun ka , kuma tun jiya da dadare na ke jin kamar wani abu ya faru da kai , shi ya sa na taho na duba in ka na lafiya " a hankali ya dan sunkuyar da kan shi ya na fadin " i'm fine , mummy ma sai da ta tambaye ni , kuma na fada mata ni lafiya ta qlau " " really you're fine ? " a hankali ya gyada mata kai kafin ya dago ya kale ta ya ce " Tell me what's wrong with you too " wani dogon nunfashi ta ja kafin ta koma baya ta konta murya cike da rauni ta ce " Mafarkin Daddy na yi " " and ! " " I really missed him , Har yanzu ba kassa yarda ya tafi ya bar mu , ko ganin karshe ban yi mishi ba " " I missed him too " ya fada cen kassa kassa mikewa zaune ta yi ta na marairaice fuska ta ce " yanzu da gaske ya tafi ba zan sake ganin shi ba , Ash ka tabbata Daddy na cikin motar nan lokacin da ta watse , kar a je ya fice kafin Explosion din " a hankali ya juyo ya kale ta ya dan girgiza mata kai kafin ya ce " Ki yi hakuri Ummi , amma Daddy ya na cikin motar , gaban ido na ya shiga cikin motar , kafin ma ya fita da ga cikin Headquater motar ta yi exploded , na duba ko ina amma ba mu samu komai ba da ga cikin gawar shi , Har yanzu wannan abun na cikin zuciya ta " wasu hawaye ne su ka fara zubo wa Ummi kamar za ta yi kuka ta ce " Shikenan yanzu ba za sake ganin Daddy na ba , why Daddy ? why za ka tafi ka barni , ni fa har yanzu ina da bukatar ka , ya ka ke so na yi yanzu " da sauri Ash ya sa hannayan shi biyu ya janyo ta jikin shi ya rungume ta ya na fadin " It's okay , ya isa haka please ki daina kukan nan , ba na jin dadin hakan " " i'm sorry bro , ba laifi na ba ne , kukan ne ya fi karfi na " " shikenan yanzu ki daina ba ga ni ba " a hankali ta yi wata yar dariya kafin ta ce " Na sani , I really love you my Twins rabin rai na " " I love you too my sister " ya fada mata kamar mai rada su na a haka su ka jiyo an rungume su a tare a rude Ash ya dago kai dan bai san ko wanene ya shigo ba wani kyawatencen murmushi Junior ya saki ya na fadin " Ohh i love you too my siblings " yar karamar dariya Ummi ta yi kamar ba ita ba ce ke shirin kuka yanzu sannan ta ce " okay , okay yanzu ku sake ni yanzu na je na yi wanka na yi breakfast yunwa na ke ji " a hankali Junior ya janye hannayan shi ya ja baya kadan ya tsaya ita ma Ummi raba jikin ta ta yi da na Ash sannan ta mike tsaye ta na fadin " see you later " ta kai karshen ta na fara takawa ta na fara takawa junior ya ce " General akwai matsala fa , yanzu Officer Lila ke ce min sun sake samun gawar wasu yaran biyu " cak Ummi ta tsaya har ta kai bakin kofa ta juyo cike da rudu ta ke cewa " Marshal maganar me ka ke yi haka ? " junior na shirin magana Ash ya riga shi cewa " ba cewa ki ka yi yunwa ki ke ji ba , yi tafiyar ki , an jima na fada miki " da to kawai ta amsa mishi kafin ta juyawar ta ta fice part din baki daya ta koma na ta part din ta na fita Ash ya kai hannu ya dauki laptop din shi , sannan ya ce ma junior " mun kusa kawo karshen wannan kungiyar kar ka damu " zama geffen shi junior ya yi kafin ya ce " General wajen two years fa mu na kan wannan Case din har yanzu ba mu samo ko wajen da su ke kashe yaran ba " dan jinkirtawa Ash ya yi kafin ya ce " kamar yadda mu ka samo da ga wani gari a ke kai yaran US , haka za mu samo wanda ke kai su " " Yanzu ya a ke ciki , tun abun bai fi karfin mu ba " junior ya fada ya na nufar sofa ya zauna " sai dai kai ya fi karfin ka , amma ba dai ni ba , Sai na kawo karshen wannan kungiyar , tun...... " kut maganar ta yanke bai kai karshen ta ba " but General ba mu san su wa su ke kai yaran US ba , at least inda ma mun san da ga wace jaha su ke tafiya da yaran ba , a ka je ba a nan su ke ba " a hankali Ash ya girgiza mishi kai ya na fadin " kar ka damu , Special suspect di na a nan kaduna ya ke , Matar da su ke aiki a tare a nan kaduna ta ke , kuma cikin unguwar nan " " kamar ya ban gane ba ? " shiru Ash ya yi bai ce komai ba har sai da ya dauki wajen good ten minutes kafin ya ajiye laptop din hannun shi saman bedside drawer ya dauki wayar shi sannan ya ce " a binciken da na yi , da sunnan aiki a ke kai yaran nan US , da na bi didigin wanda ke kai su US nan na gano cewa akwai wani seat na kungiyar a nan cikin kaduna " da karfi Junior ya ce " what , da gaske ? yanzu ka samo inda seat din ya ke , ta yadda za mu kai musu hari cikin duhu " shiru Ash ya yi bai ce mishi komai ba shi ma dai junior shiru ya yi bai ce komai ba , ya san Ash ba ya son a na maimaita mishi tambaya , shi ya sa ya yi shiru har lokacin da ya ga dama ya ba shi amsa sai da ya dauki lokaci kafin Ash ya bude baki a hankali ya ce " Je ka kawo min fruits " yar karamar dariya Junior ya yi kafin ya ce " ashe dai General ba ya supporting yunwa " ya na gama fadar haka ya tashi ya fice dakin ▪HAYAT 💦 Misalin karfe 8 cib ta farka da ga barcin ta , ko da ta farka ta shiga ta yi wanka , ta meda gown din ta , da hijab din ta fari sannan ta fito dakin ko lotion ba ta shafa ba ta na shigowa parlourn ta ji gaban ta ya yi wata mumunar faduwa amma haka ta ci gaba da takowa ta karaso ta na sallama a tare Hajiyah da wannan mutun su ka amsa mata sallamar ta sai washe baki ya ki cikin zuciyar shi ya na fadin " an ya zan iya kai musu yarinyar nan haka kawai , ya kamata na dan taba gaskiya " ya yi nisa cikin tunanin shi ya jiyo Muryar Hajiyah ta na fadin " Ta na gaishe ka ba ka ji ba ? " a razane ya dawo cikin hayacin shi ya na fadin " eh eh , yawwa sannun ki yarinya " dan sunkuyar da kai Hayat ta yi cikin zuciyar kuma ta na tsara shirin da ta yi musu a haka Hajiyah ta ce mata " Hayat wannan abokin aiki na ne , yau din nan ya dawo da ga Dubaï " a hankali Hayat ta dago kai ta mishi kallon kassan ido murya cen kassa kassa ta ce mishi " sannu da zuwa , " wani cool murmushi ya saki ya na gyada kan shi kafin ya kali Hajiyah ya ce " Ina kuma ki ka samu kyakyawar yarinya haka , a sani na dai yaron ki guda " yar karamar dariya Hajiyah ta yi kafin ta ce " ɗiyar din wata abokiya ta ce wlh " a dubu dari Hayat ta dago kai ta na kallon Hajiyah ta na zaro idanu cikin zuciyar ta ta na fadin " ku ji shegiyar mata yaushe na zama ɗiyar abokiyar ki kuma " ta na a haka ta jiyo Muryar mutumin nan ya na fadin " oh ki ce hutu a ka zo miki , ya yi kyau gaskia , sannu fa daughter " a hankali Hayat ta meda kan ta ta sunkuyar cikin zuciyar ta kuma ta na fadin " munafiki kai ka san minene Dauda din da ka ke cewa " ganin ba ta ce komai ba ya sa mutuman nan cewa " Hajiyah yarinyar ta ki fa akwai ta da kunya , shikenan , yau dai ina da aiki sosai wlh da ga nan ma Abuja na yi , amma in sha Allah jibi zan dawo mu tafi shan ice cream " kamar Hajiyah ba ta san da maganar ba kawai sai ta ce " kar ka wahalar da kan ka , na san aikin ka ba ka samun isashen lokacin ka , dan haka mun yahe maka " " no kar ki damu ai ba wata matsala ba ce , jibi ina dawowa da ga Abuja sai mu tafi har shopping ma sai mu wuce ko ba haka ba daughter na " ya kai karshen ya na kallon face din Hayat [28/12 à 08:03] 🪷🩷: MY BOOK IS ONLY ₦300 VIA 8081129487 Khadija Sabi'u Monie point bank KU TURA SHAIDAR BIYAN TA WANNAN NUMBER +22795577612 or +22798999753 اللَّهُمَّ صَلِّ عَلَى مُحَمَّدٍ وَعَلَى آلِ مُحَمَّدٍ، كَمَا صَلَّيْتَ عَلَى إِبْرَاهِيمَ وَعَلَى آلِ إِبْرَاهِيمَ، إِنَّكَ حَمِيدٌ مَجِيدٌ، اللَّهُمَّ بَارِكْ عَلَى مُحَمَّدٍ وَعَلَى آلِ مُحَمَّدٍ، كَمَا بَارَكْتَ عَلَى إِبْرَاهِيمَ وَعَلَى آلِ إِبْرَاهِيمَ، إِنَّكَ حَمِيدٌ مَجِيدٌ❤️ BISMILLAHIRRAHMANIRRAHIM FREE PAGE ............9.........❤🥂 cikin konciyar hankali Ash ya ce mata " mummy ke fa ki ka ce na fada miki abun da ke damu na " mikewa tsaye Nihal ta yi ta nufi hanyar fita dakin ta na fadin " Wlh Ash ka ci uwar raina min hankali sama da Vedad ma , amma bar ka , zai yi maganin ka " ta na gama fadar haka ta fice dakin Da kallo ya raka ta har sai da ta fice dakin sannan ya tashi a hankali ya shige dressing room Nihal kuwa kai tsaye parlourn kassa ta sauko , nan ta isko Vedad da Iqbal su na zaune abin su Vedad na ganin Nihal ya tashi da sauri ya nufe ta ya na fadin " mummy mu tafi shan ice cream please , tun da mu ka zo har yanzu ba mu fita ba , kuma ni ina son mu fita na ga gidan da ku ka zaune ka da Daddy " ya kai karshen cikin shagwaba dan karamin murmushi ta yi kafin ta ce " shikenan je ka cewa Felix ya shirya za mu fita " ba ta gama rufe bakin ta ba ya juya da gudu ya fice parlourn , a hankali shi ma Iqbal ya mike ya bi bayan shi , dan ya gaji da zama cikin gidan su na fita Nihal ta ci gaba da takawar ta , ta nufi corridor ta shiga part din ta ba ta yi five minutes ba ta fito rike da wata yar bag , da face mask ta fice parlourn ta na fitowa sai saman wata dankareriar mota fara kal mai mugun kyau an yi parking din ta dai'dai kofar shigowa parlourn , Iqbal na mazaunin driver , Vedad na geffen shi dan karamin murmushi ta saki kafin ta karaso wajen motar ta shiga gidan baya ta na fadin " Ba tare da Felix za mu tafi ba ? " tada motar Iqbal ya yi su ka bar wajen ya na fadin " no mummy , ni na ce ya yi zaman shi " da okay kawai Nihal ta amsa mishi , da ga haka ya danna hanci motar waje ya na tambayar Nihal ina za su yi , nan ta ke ce mishi ya yi dama , ba musu ya yi dama su ka bar wajen ▪ASH 🔥 bayan ya Fitar Nihal da ga Bedroom din ya tashi ya shiga dressing room jim kadan ya fito sanye da Trouser black color da T-shirt white color , ya daure wanan curly hair din na shi a baya , Kafafun shi babu takalmi a ciki sai tashin fitinannan kamshi yake yi ya na fitowa ya nufi bed din shi ya zauna ya dauki laptop din shi ya shiga aikin shi bai yi five minutes ba da Zama Ummi ta shigo ta na sallama kassa kassa , ta sanye da kayan barcin ta , Duk gashin ta a tirje ya ke , da allamun ko wanka ba ta yi ba ba tare da ya dago kan shi ba ya amsa mata sallamar ta cen kassan makoshi a hankali ta karaso geffen shi ta zauna sannan ta yi baya ta konta a hankali ya bude bakin shi ya ce " What's wrong ? " wani dogon nunfashi ta yi kafin ta ce " nothing ! " ta fada a takaice da ya ke ya san yar uwar ta shi , ya san ba karamin abu ba zai kawo ta wajen shi tun da safe haka ko wanka ba ta yi ba a hankali ya ajiye laptop din shi saman bedside drawer , ya juyo kai a hankali ya kale ta ya ce " Oya stand Up , tell me what's wrong with you ? " dan karamin gunguni ta yi kafin ta mike zaune ta na sunkuyar da kai ta ce " ta ya ka san da akwai wani abu ? " dan jinkirtawa ya yi kafin ya ce " don't forget you are my twins , Idan wani abu na damun ki , ina iya jin shi a jiki na " dan karamin murmushi ta yi ta na fadin " It's true , ka na iya jin abun da ke damu na , ni ma ina iya jin abun da ke damun ka , kuma tun jiya da dadare na ke jin kamar wani abu ya faru da kai , shi ya sa na taho na duba in ka na lafiya " a hankali ya dan sunkuyar da kan shi ya na fadin " i'm fine , mummy ma sai da ta tambaye ni , kuma na fada mata ni lafiya ta qlau " " really you're fine ? " a hankali ya gyada mata kai kafin ya dago ya kale ta ya ce " Tell me what's wrong with you too " wani dogon nunfashi ta ja kafin ta koma baya ta konta murya cike da rauni ta ce " Mafarkin Daddy na yi " " and ! " " I really missed him , Har yanzu ba kassa yarda ya tafi ya bar mu , ko ganin karshe ban yi mishi ba " " I missed him too " ya fada cen kassa kassa mikewa zaune ta yi ta na marairaice fuska ta ce " yanzu da gaske ya tafi ba zan sake ganin shi ba , Ash ka tabbata Daddy na cikin motar nan lokacin da ta watse , kar a je ya fice kafin Explosion din " a hankali ya juyo ya kale ta ya dan girgiza mata kai kafin ya ce " Ki yi hakuri Ummi , amma Daddy ya na cikin motar , gaban ido na ya shiga cikin motar , kafin ma ya fita da ga cikin Headquater motar ta yi exploded , na duba ko ina amma ba mu samu komai ba da ga cikin gawar shi , Har yanzu wannan abun na cikin zuciya ta " wasu hawaye ne su ka fara zubo wa Ummi kamar za ta yi kuka ta ce " Shikenan yanzu ba za sake ganin Daddy na ba , why Daddy ? why za ka tafi ka barni , ni fa har yanzu ina da bukatar ka , ya ka ke so na yi yanzu " da sauri Ash ya sa hannayan shi biyu ya janyo ta jikin shi ya rungume ta ya na fadin " It's okay , ya isa haka please ki daina kukan nan , ba na jin dadin hakan " " i'm sorry bro , ba laifi na ba ne , kukan ne ya fi karfi na " " shikenan yanzu ki daina ba ga ni ba " a hankali ta yi wata yar dariya kafin ta ce " Na sani , I really love you my Twins rabin rai na " " I love you too my sister " ya fada mata kamar mai rada su na a haka su ka jiyo an rungume su a tare a rude Ash ya dago kai dan bai san ko wanene ya shigo ba wani kyawatencen murmushi Junior ya saki ya na fadin " Ohh i love you too my siblings " yar karamar dariya Ummi ta yi kamar ba ita ba ce ke shirin kuka yanzu sannan ta ce " okay , okay yanzu ku sake ni yanzu na je na yi wanka na yi breakfast yunwa na ke ji " a hankali Junior ya janye hannayan shi ya ja baya kadan ya tsaya ita ma Ummi raba jikin ta ta yi da na Ash sannan ta mike tsaye ta na fadin " see you later " ta kai karshen ta na fara takawa ta na fara takawa junior ya ce " General akwai matsala fa , yanzu Officer Lila ke ce min sun sake samun gawar wasu yaran biyu " cak Ummi ta tsaya har ta kai bakin kofa ta juyo cike da rudu ta ke cewa " Marshal maganar me ka ke yi haka ? " junior na shirin magana Ash ya riga shi cewa " ba cewa ki ka yi yunwa ki ke ji ba , yi tafiyar ki , an jima na fada miki " da to kawai ta amsa mishi kafin ta juyawar ta ta fice part din baki daya ta koma na ta part din ta na fita Ash ya kai hannu ya dauki laptop din shi , sannan ya ce ma junior " mun kusa kawo karshen wannan kungiyar kar ka damu " zama geffen shi junior ya yi kafin ya ce " General wajen two years fa mu na kan wannan Case din har yanzu ba mu samo ko wajen da su ke kashe yaran ba " dan jinkirtawa Ash ya yi kafin ya ce " kamar yadda mu ka samo da ga wani gari a ke kai yaran US , haka za mu samo wanda ke kai su " " Yanzu ya a ke ciki , tun abun bai fi karfin mu ba " junior ya fada ya na nufar sofa ya zauna " sai dai kai ya fi karfin ka , amma ba dai ni ba , Sai na kawo karshen wannan kungiyar , tun...... " kut maganar ta yanke bai kai karshen ta ba " but General ba mu san su wa su ke kai yaran US ba , at least inda ma mun san da ga wace jaha su ke tafiya da yaran ba , a ka je ba a nan su ke ba " a hankali Ash ya girgiza mishi kai ya na fadin " kar ka damu , Special suspect di na a nan kaduna ya ke , Matar da su ke aiki a tare a nan kaduna ta ke , kuma cikin unguwar nan " " kamar ya ban gane ba ? " shiru Ash ya yi bai ce komai ba har sai da ya dauki wajen good ten minutes kafin ya ajiye laptop din hannun shi saman bedside drawer ya dauki wayar shi sannan ya ce " a binciken da na yi , da sunnan aiki a ke kai yaran nan US , da na bi didigin wanda ke kai su US nan na gano cewa akwai wani seat na kungiyar a nan cikin kaduna " da karfi Junior ya ce " what , da gaske ? yanzu ka samo inda seat din ya ke , ta yadda za mu kai musu hari cikin duhu " shiru Ash ya yi bai ce mishi komai ba shi ma dai junior shiru ya yi bai ce komai ba , ya san Ash ba ya son a na maimaita mishi tambaya , shi ya sa ya yi shiru har lokacin da ya ga dama ya ba shi amsa sai da ya dauki lokaci kafin Ash ya bude baki a hankali ya ce " Je ka kawo min fruits " yar karamar dariya Junior ya yi kafin ya ce " ashe dai General ba ya supporting yunwa " ya na gama fadar haka ya tashi ya fice dakin ▪HAYAT 💦 Misalin karfe 8 cib ta farka da ga barcin ta , ko da ta farka ta shiga ta yi wanka , ta meda gown din ta , da hijab din ta fari sannan ta fito dakin ko lotion ba ta shafa ba ta na shigowa parlourn ta ji gaban ta ya yi wata mumunar faduwa amma haka ta ci gaba da takowa ta karaso ta na sallama a tare Hajiyah da wannan mutun su ka amsa mata sallamar ta sai washe baki ya ki cikin zuciyar shi ya na fadin " an ya zan iya kai musu yarinyar nan haka kawai , ya kamata na dan taba gaskiya " ya yi nisa cikin tunanin shi ya jiyo Muryar Hajiyah ta na fadin " Ta na gaishe ka ba ka ji ba ? " a razane ya dawo cikin hayacin shi ya na fadin " eh eh , yawwa sannun ki yarinya " dan sunkuyar da kai Hayat ta yi cikin zuciyar kuma ta na tsara shirin da ta yi musu a haka Hajiyah ta ce mata " Hayat wannan abokin aiki na ne , yau din nan ya dawo da ga Dubaï " a hankali Hayat ta dago kai ta mishi kallon kassan ido murya cen kassa kassa ta ce mishi " sannu da zuwa , " wani cool murmushi ya saki ya na gyada kan shi kafin ya kali Hajiyah ya ce " Ina kuma ki ka samu kyakyawar yarinya haka , a sani na dai yaron ki guda " yar karamar dariya Hajiyah ta yi kafin ta ce " ɗiyar din wata abokiya ta ce wlh " a dubu dari Hayat ta dago kai ta na kallon Hajiyah ta na zaro idanu cikin zuciyar ta ta na fadin " ku ji shegiyar mata yaushe na zama ɗiyar abokiyar ki kuma " ta na a haka ta jiyo Muryar mutumin nan ya na fadin " oh ki ce hutu a ka zo miki , ya yi kyau gaskia , sannu fa daughter " a hankali Hayat ta meda kan ta ta sunkuyar cikin zuciyar ta kuma ta na fadin " munafiki kai ka san minene Dauda din da ka ke cewa " ganin ba ta ce komai ba ya sa mutuman nan cewa " Hajiyah yarinyar ta ki fa akwai ta da kunya , shikenan , yau dai ina da aiki sosai wlh da ga nan ma Abuja na yi , amma in sha Allah jibi zan dawo mu tafi shan ice cream " kamar Hajiyah ba ta san da maganar ba kawai sai ta ce " kar ka wahalar da kan ka , na san aikin ka ba ka samun isashen lokacin ka , dan haka mun yahe maka " " no kar ki damu ai ba wata matsala ba ce , jibi ina dawowa da ga Abuja sai mu tafi har shopping ma sai mu wuce ko ba haka ba daughter na " ya kai karshen ya na kallon face din Hayat [29/12 à 11:23] 🪷🩷: MY BOOK IS ONLY ₦300 VIA 8081129487 Khadija Sabi'u Monie point bank KU TURA SHAIDAR BIYAN TA WANNAN NUMBER +22795577612 or +22798999753 ❤👑 MALLAKIN MEERAH 👑❤ اللَّهُمَّ صَلِّ عَلَى مُحَمَّدٍ وَعَلَى آلِ مُحَمَّدٍ، كَمَا صَلَّيْتَ عَلَى إِبْرَاهِيمَ وَعَلَى آلِ إِبْرَاهِيمَ، إِنَّكَ حَمِيدٌ مَجِيدٌ، اللَّهُمَّ بَارِكْ عَلَى مُحَمَّدٍ وَعَلَى آلِ مُحَمَّدٍ، كَمَا بَارَكْتَ عَلَى إِبْرَاهِيمَ وَعَلَى آلِ إِبْرَاهِيمَ، إِنَّكَ حَمِيدٌ مَجِيدٌ❤️ BISMILLAHIRRAHMANIRRAHIM PAGE ............10.........❤🥂 a hankali Hayat ta gyada mishi kai ba tare da ta dago ba murmushi mai dan sauti Hajiyah ta yi kafin ta ce " to shikenan Allah ya kai mu jibin " " hmmm , ai ku da ga nan sai lahira , gobe ma ba za ku gan ta ba " Hayat ta fada cikin zuciyar ta ta na gama fadar haka ta mike tsaye ba tare da ta ce komai ba ta nufi hanyar dining room da sauri Hajiyah ta ce mata " Hayat ina kuma za ki je " a hankali Hayat ta juyo ta saki wani cool murmushi ta ce " Ruwa ne zan sha " da to kawai Hajiyah ta amsa mata , ita kuma Hayat ta juya ta ci gaba da tafiyar ta ta shige kitchen ta na shiga ta fara bin wajen da kallo , a hankali ta fara takawa kamar barauniya , ta dinga bude duk closet din kitchen din , a hankali da allamun akwai abun da ta ke nema ta bude wajen closet uku kafin ta saki wani kyawatencen murmushi ta kai hannu ta dauki kwalin match din da ta gani da sauri ta juya bayan ta , ta na kallo kar a je Hajiyah ta taho , amma sai ta ga ba kowa da sauri ta ci gaba da bude sauran closet din har sai da bude su duka ba ta samu abun da ta ke so ba , kamar za ta yi kuka cen ta hango wani dan karamin Space tsakanin fridge da wani closet a hankali ta karaso wajen ta na rokon Allah ya sa ta samu abun da ta ke nema ai ko cikin sa'a tun kafin ta duba idanun ta su ka hango mata wani Jug fari , da wani abu cikin me color blue da sauri ta karaso wajen ta dauki Jug din , ta daura saman closet ta sa hannu ta bude murfin da sauri sauri ta kai hancin ta ta shinshina da sauri ta janye ta na sakin wani cool murmushi , tabass gasoline ne ( To fa me ta ke shirin yi da Essence har da ashana 🤔🤔 ) ko rufe bidon ba ta yi ba ta dauke shi ta nufi door ta baya ta fice kitchen din ta fito bayan gidan ta na fitowa ta fara zazzaga gasoline din a wajen , ta na tafiya ya na zuba kamar igiya , haka har ta karaso wajen motocin Hajiyah da ta mutumin nan su ma sai da ta dan watsa musu kadan , sannan ta nufi hanyar fita gidan dai'dai ko ta kawo bakin kofar gasoline din ya ida ta na ganin ya ida ta tila bido din gefe ta riko kwallin ashanar nan ta bude ta ciro guda , ta fara gyasta wa amma ta ki kamawa , har ta yadda ta , ta ciro wata ita ma ta ki kamawa kamar za ta yi kuka ta ce " haba don Allah kar ki yi min haka " ta kai karshen ta na yadda ta hannun ta ta ciro uku lokaci guda kamar da ga sama ta jiyo Muryar mutumin nan ya na fadin " ke , ke me ki ke yi haka ? " ya fada da dan karfi ,ya na fara takawa ya nufe ta , dan ya karaso bakin kofar parlourn zai fito ya jiyo warin gasoline din a dubu dari Hayat ta shiga gyasta ashanar nan , har kuka ya kubce mata cikin sa'a ko , ko taku uku na kirki bai yi ba ashanar nan ta kama wani cool murmushi Hayat ta saki hawaye na zubo mata , ta tila Ashanar nan saman Gasoline din da ta zuba nan take ko ya kama da wuta , ya bi hanyar da ta zuba shi har saman motocin nan ta na ganin ya kama ta juya da gudu ta bude kofar gidan ta fice , ta janyo kofar ta rufe ta ta baya ta na fadin " Allah ya isa la'anannu , mazinata kawai , ku kone baki daya " ta fada da karfi ta na barin wajen da gudu ko hanjar da za ta bi ba ta sani ba ita kawai ta tafi shi dai mutumin nan ya kassa motsi wutar duk ta zagaye hanyar fita gidan da gudu Hajiyah ta fito ta na fadin " Lafiya me ke faruwa " cike da bacin rai mutumin nan ya ce " ban sani ba , ba ki da idanu ne , yarinyar nan da ki ka kawo ita ce ta saka wa gidan wuta kuma ta gudu " da gudu Hajiyah ta nufi kofar fita gidan , sai dai ina wutar har ta yi karfi ta mamaye ko ina , ga kuma Hayat ta rufe kofar gidan ta baya , babu yadda za a yi su tsira , sai dai na ce Allah ya cece ku dan gaskia ba ku da hanyar tsira a nan , ga gidan kuma da motoci har biyu , su ma sun kama da wuta , ga kuma gas a kitchen , to fa ▪NIHAL 🥀 Tafiyar su su ke yi cikin konciyar hankali saman hanyar , har yanzu ba su yi kwana ko guda ba a hankali Iqbal ya dan juyo da kan shi ya kali Nihal ya ce " mummy wai har yanzu ba za mu yi kwana ba ? " yar karamar dariya Nihal ta yi kafin ta ce " To , ni ma ban sani ba , kun san fa yanzu shekara 30 rabo na da kaduna ka san ba komai zai tsaye a yadda na bar shi ba " da sauri Vedad ya juyo ya na fadin " mummy ba dai ba ki san hanya ba , kar mu bace fa " ya kai karshen kamar zai yi kuka girgiza mishi kai Nihal tayi ta na fadin " no ba za mu bace ba , mu da mu ke da Ash , ko mun bace zai samo mu , bare ma ba za mu bace ba , Iqbal yi kwanar cen ta biyu " gyada mata kai ya yi ya na fadin " to mummy Allah dai ya sa ba bacewa mu ka yi ba " yar karamar dariya Nihal ta yi , dai'dai lokacin da su ka yi kwanar ba shiri Iqbal ya ja wani wawan burki samakon mutumin da ya buge , har sai kan Vedad ya bugu a gaban motar a razane Nihal ta ke kallon Iqbal ta ce " Iqbal lafiya za ka yi irin wannan burki " sai zaro idanu Iqbal ya ke yi a rude ya ke fadin " mummy mutun na buge , wlh ban gan ta ba , kawai sai ganin na yi ta fada saman motar mummy wlh ban gan ta ba " ya kai karshen kamar zai yi kuka " inallillahi " Nihal ta fada da dan karfi ta na zame belt din ta ta bude kofar motar ta sauko da gudu ta nufi Hayat da ke konce wanwar gaban motar ta bugu sosai a kai har jini ta ke zubar wa a rude Nihal ta Zube saman guyiwowin ta gaban Hayat ta na ƙare mata kallo dago kai ta yi ta kali Iqbal ta ce " sauko ka sa ta cikin mota , mu tafi gida Ummi ta duba ta " a dubu dari Iqbal ya sauko da ga cikin motar ya nufi Hayat da ke konce a kassa ya sa hannayan shi duka biyu ya dauke ta cak , sannan ya juya ya nufi motar da sauri Nihal ta sha gaban shi ta bude mishi gidan baya , ya kontar da ita a ciki sannan Nihal ta rufe kofar ta zagayo daya geffen ta bude ta shiga , shi kuma Iqbal ya shiga mazaunin driver ya tada motar ya juya su ka kama hanyar komawa gida a hankali Nihal ta sa hannu ta janyo Hayat ta kontar da kan ta saman cinyar ta ta na kallon face din ta " mummy i'm so sorry wlh ban gan ta ba , ni ban ma san da ga ina ta fado ba " Iqbal ya fada kamar zai yi kuka mika hannun ta ta yi ta dafa shoulder din shi cikin sigar rarrashi ta ce " don't worry , ba abun da zai faru " ta na gama rufe bakin ta Vedad ya ce " mummy duba kar a je ta mutu " " no kar ka damu , ba ta mutu ba kawai ta dan ji rauni ne a kai " kallon dawo da kallon shi kan Iqbal ya ce " kar ka damu big bro punishment kawai zai ba ka , ba zai sa a rufe ka ba " wata muguwar hararra ta kassan ido Iqbal ya wurga ma Vedad , ya na neman ya saka shi cikin wata sabuwar matsalar Nihal kuwa a hankali ta sa hannu ta zare mata dan karamin hijab din ta , ta daura a wajen da ke zubar da jini , ta toshe da ga haka ba wanda ya sake cewa komai har su ka iso gida ko da su ka shiga gidan ba nufi parking space ba , kai tsaye bakin kofar parlourn ya nufa da motar ya yi parking din ta sannan ya bude kofar shi zai sauka ya ce ma Vedad " yi sauri je ka kira Ummi ta fito " ya na gama fadar haka ya sauko da ga cikin motar shi ma Vedad sauka ya yi da ga cikin motar ya nufi cikin gidan da gudu Iqbal kuwa ya bude gidan baya ya sa hannayan shi duka biyu ya dauko Hayat ya nufi cikin gidan ita ma Nihal saukowa ta yi ta bi bayan shi da sauri ta su ka shiga cikin gidan su na shiga ya kontar da Hayat saman Sofa three seaters sannan ya koma gefe ya tsaya ya na kallon ta Nihal na shirin magana , Vedad ya fito da gudu da ga cikin corridor ya na fadin " mummy , Ummi ta na cikin wanka " dafe kan ta Nihal ta yi ta na zama saman sofa ta na fadin " Wayoooooo ni Allah , yanzu ya za mu yi , kar ta zubar da jini dayawa , mu je ta samu matsala " shi dai Iqbal tsaye ya yi ya na kallon Hayat Nihal na Kamala maganar ta , ta ga Iqbal ya juya da gudu ya nufi stair ya Haye , ya na Hayewa ko Junior ya fito da ga cikin dining room ya na rike da tray din fruits ya na ganin Hayat ya ajiye tray din hannun shi saman dining table din ya nufi parlourn da sauri ya na fadin " mummy me ya faru ne " cikin ko in kula Vedad ya ce " ba Iqbal ba ne ya buge ta da mota " shiru Junior ya yi ya na kallon Hayat ba tare da ya ce komai ba , Nihal dai ta na dafe da kai ta lumshe idanun ta bangaran Iqbal kuwa ya na Hayewa stair ya nufi part din Ash kai tsaye tun da ga parlourn shi ya fara kwalla mishi kira har sai da ya shigo cikin bedroom din babu ko sallama tun kiran farko da ya yi Ash ya ji shi amma bai yi ko motsi ba , ya na nan zaune yadda junior ya bar shi ya na rike da wayar shi da sauri Iqbal ya karaso gaban shi ya na fadin " Big bro don Allah taso mu tafi " cikin nitsuwa Ash ya ajiye wayar shi saman bedside drawer ya dago kai ya kali Iqbal ya ce " What happening ? " " Vedad ya je kiran Ummi ta shiga wanka , kuma ta na zubar da jini dayawa , please tashi mu tafi ka duba ta " Iqbal ya fada duk ya bi ya rude " okay calm down your mind , Fada min me ke faruwa " a hankali Iqbal ya ja wani dogon nunfashi ya na saukewa kafin ya ce " mun fita ne tare da mummy da Vedad , shi ne na zo zan yin kwana na buge wata yarinya , kuma ta ji ciwo a kan ta , yanzu haka ta na parlour ta na zubar jini sosai , shi ne Vedad ya je kiran Ummi amma ta shiga wanka , mu je ka duba ta please " ya kai karshen ya na marairaice fuska a hankali Ash ya kai hannu ya bude box din bedside drawer ya dauki A box sannan ya mike , cike da nitsuwa ya fara takawar shi kamar ba ran mutun ne ba ke cikin hatsari , ya fice dakin Iqbal na biye da bayan shi a haka su ka sauko stair su ka karaso cikin parlourn Nihal na ganin shi ta mike ta na fadin " yawwa Ash don Allah duba mana ita har yanzu ba ta farka ba " ta kai karshen ta na nuna mishi Hayat da sauri Vedad da Junior su ka koma geffen su ka ba shi waje a hankali ya karaso ya ajiye A box din hannun shi saman table sannan ya juya ya kali Hayat ta na shirin Dauke mata Hijabin da Nihal ta daure a kai har ya mika hannun shi ya tsaya cak ya na kallon face din ta wata irin muguwar Faduwa Gaban shi ya yi har sai da yan dan zaro idanun shi da sauri ya janye hannun shi ya yi baya kadan ya na ci gaba da kallon face din ta babu ko kiftawa cike da rudu Nihal ta ce mishi " Ash Lafiya ka tsaya , da yi mata dressing wajen mana , tun ba ta zubar da jini sosai ba " a hankali Ash ya girgiza mata kai ya na fadin " no mummy ba zan iya duba ta ba " ya na gama fadar haka ya juya ya nufi stair ya Haye da sauri sai kwalla mishi kira Nihal ta ke yi amma ina ko juyowa bai yi ba ya na Hayewa stair din Ummi ta fito da ga cikin corridor kai a sunkuye ta na latsa wayar ta , ta na fadin " My angel lafiya ka ke nema na haka " Vedad na jiyo Muryar ta ya nufe ta da gudu ya riko hannun ta ya na fadin " Ummi mu tafi don Allah ki duba ta , big bro ya ce shi ba zai duba ta ba " ya kai karshen ya na jan hannun ta su ka nufi parlour cike da rudu ta ce mishi " My angel tsaya mana kar ka cire min hannu me ya k...... " kut maganar ta yanke idanun ta su ka sauka kan Hayat da sauri ta kwace hannun ta , ta nufi Hayat ta Zube saman guyiwowin ta gaban sofar ta na kallon ta ce " mummy me ya faru ne ? " wata nanauyar ajiyar zuciya Nihal ta sauke har sai da Iqbal da ke tsaye geffen ta ya juyo ya kale ta , sannan ta ce " Ummi please ki duba ta , na kira Ash ya duba ta amma ya ce ba zai iya ba " " okay mummy ku kawo min A box " ta fada da sauri Junior ya dauki A box din da Ash ya ajiye saman table ya mika wa Ummi sannan ya kai hannu zai dauki Hayat da sauri ta ce mishi " wait me ka ke shirin yi " " zai kai miki ita ne part din ki " ya fada ya na janye hannayan shi " no barta , kar a motsa ta dayawa , ku ban waje kawai " ta fada ta na bude A box din ta ajiye kassa gefe ta juyawa Nihal ta yi ta nufi part corridor ta shige , ta nufi part din ta Shi ma junior juya wa ya yi , ya nufi Dining room ya dauki tray din Fruits din shi ya nufi stair ya Haye ya nufi part din Ash Iqbal da Vedad kuma a nan su ka tsaya su na kallon ta , har sai da ta gama yi wa Hayat dressing din wajen da ta bugu , ta yi mata wasu allurai sannan ta nufi Sofar gefe ta zauna , sannan ta ce ma Iqbal ya dauki Hayat ya kai ta Dayan bedroom na Part din ta ba musu ya dauke ta ya nufi corridor , shi kuma Vedad ya koma geffen ta ya zauna ya na faman turo baki yar karamar dariya Ummi ta yi kafin ta ce " To wa kuma ya Tabba min My angel ? " " Sister , ni na yi fushi da Iqbal , ice cream fa mu ka tafi sha , kawai ya buge yarinyar nan , yanzu ga shi mun dawo gida ni ban sha ice cream di ta ba " ya na gama fadar haka Iqbal ya fito da ga corridor ya nufi stair zai Haye da sauri Ummi ta ce mishi " Iqbal come here one minute " ba musu ya juyo ya dawo cikin parlourn ya karaso gaban ta ya tsaya ya na fadin " what happening , ina son na je na yi wanka " " kar ka damu ba za mu jima ba , kneel down " Ta fada mishi cikin ba da umarni dan zaro idanu Iqbal ya yi ya na kallon ta ya ce " kneel down kuma ? " " za ka yi kneel down ko sai na tashi gare ka " Ummi ta fada da dan karfi dan karamin gunguni ya yi kafin ya Zube saman guyiwowin shi a hankali ya daga hannayan shi sama " Kai , ya a ka yi ka buge yarinyar nan , a sani na dai ka na da driver's license " da sauri Vedad ya karbe zancen da cewa " kuma fa ice cream mu ka tafi Sha , ni ice cream di ta na ke so " ya kai karshen cikin shagwaba yar karamar dariya Ummi ta yi kafin ta ce " Shikenan calm down My angel , yanzu Fadi wane irin punishment za mu ba shi ? " dan zaro idanu Iqbal ya yi ya na kallon Ummi ya ce " No wace punishment kuma , no ba laifi na ne ba fa , ni ban ma san da ga ina ta fito ba " " okay za ka san da ga ina ta fito in General ya kama ka , Ba kai ba ka tuki da kyau ba " " kuma Sister gudu fa ya ke yi da mota , sai da mummy ta ce mishi ya yi a hankali " Vedad ya fada ya na kumshe dariya " Vedad ba na son Karya , yaushe na yi gudu cikin muto , ka ji tsoron Allah " Iqbal ya fada ya na neman ya kare kan shi , kowa ya san ba haka ta faru ba " Sister duba forehead di na ki na gani , har ni sai da na buge kai na " Ya fada cikin shagwaba ya na nuna wa Ummi forehead din shi hannu Ummi ta kai ta dan janye gashin gaban goshin shi , nan ya ga wajen har ya yi ja kun san dai farar fata yadda ta ke " Laaa My angel , shi ya yi maka haka , eh lalle yau Iqbal zai sha punishment , musaman General zan kiro " shagwabe fuska Vedad ya yi ya na fadin " uhmm uhmm , kuma sai ya sayo min ice cream , ni ice cream na ke so " Kukan shagwaba shi ma Iqbal ya shiga yi ya na fadin " uhm uhm uhm , ni ku kyale ni ba abun da na yi , kariya fa ya ke miki " " yi min shiru , Ta ya a ka yi forehead din shi ya yi ja kuma , shi ya buge kan shi , tashi ka fara Frog jump kafin mu kai ka wajen General " Ummi ta fada cikin tsare gida allamun ba wassa ta ke ba wata yar karamar dariya Vedad ya yi ya na fadin " yawwa sister , ni bari ma na je na kira big bro , kuma , kuma ki ce mishi sai ya yi min Pancakes , yau da fruits kawai na yi breakfast " ya kai karshen cikin shagwaba daura hannun ta Ummi ta yi saman kumatun shi cikin sigar rarrashi ta ce mishi " ohhhh sorry my Angel , tashi ka je ka yi wanka , kafin ka dawo ya yi maka " wani cool murmushi Vedad ya saki kafin ya tashi da gudu ya Haye stair ya na yar dariya sai da ya bar wajen sannan Iqbal ya ce " Uhm uhm ,ni fa ba da gangan na buge ta ba , asali ma ni ganin ta kawai na yi ta fado saman motar " " oh ka na nufin da ga sama ta fado ? " Ummi ta fada ta na daga mishi gera guda marairaice fuska Iqbal ya yi kafin ya ce " ni ma ban sani ba , ku bari har ta tashi ta fada miki abun da ya faru , kin san fa halin Vedad da son kara ma miya gishiri " " amma ai kai ka ke tukin , mazza tashi ka fara frog jump " " what , No gaskiya ba zan yi ba , haba na gaji wlh , na san kuma sai kun fadawa big bro shi ma ya ce sai ya kara min punishment " ya fada kamar zai yi kuka dariya sosai Ummi ta yi har sai da idanun ta su ka kawo ruwa sai da ta tsagaita dariyar ta sannan ta ce " Dan rainin sens kawai , mazza tashi ka yi wa My angel Pancakes din shi , in kuma ka ki na fadawa General " mikewa tsaye ya yi ya na murmushi ya dawo Geffen ya zauna ya na fadin " yawwa sister shi ya sa na ce kin fi big bro kirki " hararrar wassa Ummi ta yi mishi ta na fadin " Rabu da yi min dadin baki tashi ka yi wa Vedad Pancakes din shi " kauda kan shi gefe ya yi ya na jingina bayan shi a jikin sofar ya na fadin " ni babu inda zan je " " ka fi kowa sanin yadda Vedad ke son Pancakes kuma ya ce ka yi mishi , dama saboda kai ba ku tafi sayan ice cream , gwara ka tashi ka yi mishi tun bai sauko ba ya fara rigimar shi " " Shikenan amma fa gaskia sai na yi wanka " " kai dai ka sani , ka san halin Vedad in bai samu abun da ya ke so ba , yanzu zai yi zaune ya aza maka kuka kamar baby , sannan kuma General ya shigo zancen dan babu wanda ya isa ya saka Vedad kuka ya zauna lafiya " " wai mi ya sa Vedad ke son Pancakes haka , Ni ma ina so amma ba kamar na shi ba " wani cool murmushi Ummi ta saki kafin ta ce " Daddy ya saba mishi da hakan , kullum breakfast din Vedad da ga Pancakes sai fruits , tun ya na baby , ko ranar da Daddy ya rasu sai da ya yi mishi sannan ya tafi , Har yanzu ina ganin ranar nan kamar jiya " ban take idanun ta su ka kawo ruwa dan murmushi mai dan sauti Iqbal ya yi kafin ya mike tsaye ya na fadin " Shikenan , bari na tafi na yi mishi , tun kafin bai sauko ba na shiga sabuwar cakwakiya , shagwababe kawai , wlh duk kun bi kun shagwaba shi , wai har da wani suna My angel " yar karamar dariya Ummi ta yi kafin ta ce " Yeah , he is our happyness , He is our Angel , na ga kai Cutie pie ka ke kiran shi " " yeah because he is so so cute " ya kai karshen ya na juyawa ya bar parlourn ya nufi dining room ya shiga kitchen [30/12 à 07:53] 🪷🩷: TAURIN ZUCIYA 💖🌺💍 ( RETURN ) ( ROMANTIC LOVE STORY )💋🔥 MY BOOK IS ONLY ₦300 VIA 8081129487 Khadija Sabi'u Monie point bank KU TURA SHAIDAR BIYAN TA WANNAN NUMBER +22795577612 or +22798999753 ❤👑 MALLAKIN MEERAH 👑❤ اللَّهُمَّ صَلِّ عَلَى مُحَمَّدٍ وَعَلَى آلِ مُحَمَّدٍ، كَمَا صَلَّيْتَ عَلَى إِبْرَاهِيمَ وَعَلَى آلِ إِبْرَاهِيمَ، إِنَّكَ حَمِيدٌ مَجِيدٌ، اللَّهُمَّ بَارِكْ عَلَى مُحَمَّدٍ وَعَلَى آلِ مُحَمَّدٍ، كَمَا بَارَكْتَ عَلَى إِبْرَاهِيمَ وَعَلَى آلِ إِبْرَاهِيمَ، إِنَّكَ حَمِيدٌ مَجِيدٌ❤️ BISMILLAHIRRAHMANIRRAHIM PAGE ............11.........❤🥂 ▪ASH 🔥 Bayan ya fice parlourn kai tsaye part din shi ya koma ya na shiga ya wuce bedroom din shi , ya meda Door din ya danna wani button a ciki nan take ta yi locked din kan ta shi kuma ya nufi bakin bed din shi ya zauna , a hankali ya yi baya ya konta , ya daura hannayan shi biyu saman face din shi ya na a haka Junior ya yi mishi knocking din kofar ya na fadin " General are you okay ? " a hankali Ash ya sauke ajiyar zuciya kafin ya mike zaune ya ce ma junior " yeah ,just let me " da to kawai junior ya amsa mishi kafin ya juya ya ajiye tray din hannun shi saman table sannan ya fice part din Ash na jin ya fara takawa ya koma ya konta ya na fuskantar ceiling a hankali ya na kifta idanun a hankali ya bude bakin murya kassa kassa ya ce " Ya Allah in har yanzu mafarkin ne na ke , ka tashe ni , na roke ka , Why za ka yi min haka ? " ya kai karshen ya na lumshe idanun shi a hankali a hankali a hankali duk sigar jikin shi ta fara shi kamar wanda ya ke cikin matsananciyar sha'awa a dubu dari ya ware idanun shi ya mike zaune , a rude ya ke fadin " wai me ya ke shirin faruwa da ni haka " ya na gama fadar haka ya kai hannun shi da sauri sauri wajen bedside drawer ya bude box din ya fido wata yar Box fara kamar A box , Ya bude ta da sauri , allurai ne cike a wajen hannu ya kai ya dauki guda , sannan ya rufe box din ya meda cikin bedside drawer sannan ya zare dan murfin nan na saman allurar , babu ko bismillah ya caka ta a damtsen shi , har sai da ya dan lumshe idanun shi kadan , sai da ya Kamala sannan ya zare ta , ya tashi ya nufi Toilet ya yarda Allurar a cikin trush sannan ya fito ya na fitowa na ga duk kamanin shi sun sauya , idanun shi sun koma jazir kamar jini duk jijiyo yin jikin shi sun fito baro baro , na gaban goshin shi har wani bul bul su ke yi kamar bugun zuciya , har wata kerma jikin shi ke yi a haka ya karaso bakin gadon shi , ya kai hannu ya dauki remote ya kashe duk lamps din dakin , ya kara gudun ac , sannan ya sa hannu ya fara cire kayan jikin shi , sai da ya rage da ga shi sai short , sannan ya Haye bed din shi ya yi rub da ciki bari dai na leko Barira may be kafin ya tashi ▪ZINDER (kauyen NAWACH KALÉ ) ▪BARIRA konce ta ke saman Tabbarma cikin harabar gidan , ta tada kai da cinyar inna , sai hawaye ta ke bibiyu ta na a haka malam ya shigo ya na sallama ta na jin sallamar shi ta mike zaune , ta na hannu ta goge hawayen ta da sauri ta ce mishi " an gan ta ne ? " shiru malam ya yi bai amsa mata ba , sai da ya karaso inda su , shi ma ya zauna saman tabarmar , Barira dai da inna sun zuba mishi idanu su na jiran ya ce wani abu sai da ya dan dauki lokaci kafin ya ce " An gan ta am...... " da sauri Barira ta katse shi da cewa " Ina take to , in an gan ta " " Barira kin bari na Kamala magana ta dai ko , Moustafa ya ce min ya gan ta lokacin da ta kama hanyar fita gari , Da farko bai gane ta ba saboda cikin dare ne , Har birni su ka tafi neman ta , ke har gidan Bus su ka tafi , cikin sa'a ko wani driver ya ce musu eh ya gan ta , kuma shi da kan shi ya dauke ta ya kai ta kano wajen Yan uwan ta " " inallillahi wa'ina illaihi raji'un , malam wane yan uwa kuma , mu kadai ne Ahalin ta fa " inna ta fada kamar za ta yi kuka ta na gama fadar haka ta ga Barira ta fadi a wajen sumamiya wata yar karamar kara inna ta saki ta na fadin " na shiga uku , Barira , Barira don Allah ki tashi , malam ka yi wani abu mana " ta fada kamar za ta yi kuka a hankali ya gyada mata kai kafin ya tashi tsaye ya nufi tulunan ruwa , ya debo kadan a cikin wani cup da ke saman guda da ga cikin sannan ya dawo inda Barira ta ke ya dan zubo kadan a hannun shi ya yarfa mata a fuska a dubu dari ta ware idanun ta , ta na mikewa zaune ta na bin su da kallo " Sannu kin ji " inna ta fada ta na daura hannu saman kumatun Barira a hankali ta bude baki ta ce " inna Hayat ta bar garin nan ? " ta na gama fadar haka ta ji malam da ke geffen ya daura hannun shi saman kan ta , cikin sigar rarrashi ya ce " Ki kontar da hankalin Barira ba abun da zai same ta , tun da har Allah ya kai ta kano lafiya , to in sha Allah ba abun da zai same ta , In sha Allah zan kira kawun ki Illo ya tura yaran shi neman ta a kano , matsalar yanzu sai na samu yadda zan tura mishi hoton ta , amma ki kontar da hankalin ki ba abun da zai same ta kin ji ko ? " a hankali ta gyada mishi kai kafin ta mike jiki ba kwari , ta nufi hanyar Dakin ta , ta na tafiya kamar me maye amma a haka ta isa dakin ta shige da kallo inna da malam su ka raka ta har sai da ta shiga sannan malam ya mike ya na fadin " bari na je ko da bakin gari ne , na samu yaron da ke da babbar waya ya tura mishi hoton ta " " Shikenan , Allah ya bada sa'a , a dawo lafiya " inna ta fada cikin sanyin murya da Amine ya amsa mata kafin ya fara takawa ya fice gidan sai da ya fita ita ma ta tashi ta nufi dakin da Barira ta shiga ta na fadin " ya Allah ka tsare mana Hayat duk inda ta ke " ta kai karshen ta na shiga dakin ▪KADUNA ( GIDAN SU NIHAL ) ▪MISALIN KARFE 8 NA DARE ▪HAYAT 💦 A hankali ta fara kokarin bude idanun ta , ta na bude su sai saman ceiling shiru ta yi ba ta motsa ba kallon ceiling kawai ta ke yi ta na kifta idanun ta a hankali sai da ta dauki wajen good ten minutes a haka kafin ta mike zaune a hankali da sauri ta kai hannu ta dafe kan ta na fadin " wayooo Allah kai na " dan ba karamar sara mata ya yi ba nan ta ji Bandejin da ke a le wajen , a hankali ta sauko da hannun ta , ta fara bin dakin da kallo sam bai mata kama da gidan Hajiyah ba , wannan ya yi biyun dakin da ta sauka a gidan Hajiyah a hankali ta matso bakin gadon ta sauko da kafafun kassa sannan ta mike tsaye ba shiri ta koma ta zauna , dan jikin ta ba kwari sam amma a haka ta aro duk jarumtar ta , ta mike tsaye ta nufi kofar fita dakin ta kai hannu ta kama handle din kofar ta jayo ta sa kafa ta fice dakin , ta fito cikin corridor din sai da ta kali damar ta , ta kali hagu sannan ta yi damar ta dan nan wajen ya fi haske sosai a haka ta biyo corridor din nan ta na tafe ta na dafe da bango , a haka har ta fito corridor din duk mutanan gidan ko su na nan Banda Ash da Junior , Vedad na faman zuba musu shagwaba , su kuma su na biye mishi su na dariya ita dai Hayat tsaya wa ta yi ta zuba musu ido ta kassa cewa komai su na a haka kawai Iqbal ya juyo ya kali wajen corridor din , kawai sai ya gan ta tsaye su na yin ido hudu da shi , ta baya kadan ta na sunkuyar da kai dan karamin murmushi ya yi kafin ya kali Nihal ya ce " Mummy " dawo da kallon ta ta yi gare shi ta na fadin lafiya da kai ya mata allamun ta kali corridor a hankali ta juya da kan ta , ta na murmushi nan ta ga Hayat tsaye ta na dafe da bango ta sunkuyar da kai kara fadada murmushin ta Nihal ta yi kafin ta mike tsaye ta fara takawa ta nufi Hayat a tare Vedad da Ummi su ka juya su ka kali Hayat wani dan karamin murmushi Ummi ta yi ta na fadin " Har kin tashi ? " ( kar fa ku manta fa duk maganar nan da su ke yi da turanci su ke yin ta " Hayat kuma ta na tsaye sai ji ta yi an kamo hannun ta sai da ta razana ta dan ja da baya " calm down ba abun da zan yi miki , mu je ko ? " Nihal ta fada ta na janyo Hayat ba musu ta biyo bayan Nihal ta na tafiya a hankali kai a sunkuye har sai da su ka karaso sofar da Nihal ta ke zaune , ta zauna sannan ta zaunar da Hayat geffen ta ta dago kai ta kali Iqbal ta ce " Je ka ce ma chef ya shirya mata jollof Rice , na san ba za ta iya cin abincin mu ba , sannan ka kawo mata fruits " da to Iqbal ya amsa mata kafin ya tashi ya nufi dining room ya shiga kitchen ya na barin wajen Nihal ta kai hannu ta dago habar Hayat ta na murmushi ta ce " Sannu ya jikin na ki " shiru Hayat ta yi ta zuba mata idanu , ita fa sam ba ta gane abun da ta ke fada ganin yadda ta yi shiru ta tsare ta da idanu ya sa Nihal gane cewar ba ta jin turanci da hausa ta ce mata " Sannu ya jikin na ki " a hankali Hayat ta gyada mata kai murmushi mai dan sauti Nihal ta yi kafin ta ce " bude baki ki yi magana ba cinye ki zan yi ba , ya sunan ki " Nihal na gama rufe bakin ta Ummi ta matso bakin sofar da ta ke zaune , da ya ke duk cikin su babu wanda bai iya hausa ba , kawai dai ba su son yin magana da ita ne , sun saba sosai da Turanci saboda shi ne a ke yi a US cikin wani kwarbaban harshen hausar ta ta ce " sannu ya jikin na ki , kan ki ba ya miki ciwo " a hankali Hayat ta gyada mata kai allamun eh , dai'dai lokacin da Iqbal ya fito da ga cikin dining room ya na rike da tray shake da Fruits kai tsaye saman table ya ajiye shi sannan ya matsa table din gaban sofar su Nihal shi ma ya koma dayan geffen Hayat , da harshen turanci ya ce mata " Hi ! ya jikin na ki ba ki dai ji ciwo ba sosai , ko akwai wani wajen da ke yi miki ciwo " sai da ya Kamala maganar shi sannan Ummi ta ce mishi " ba ta jin turanci yi mata da hausa " " okay , san...nu ya jikin na ke " Iqbal ya fada a rarabe allamun bai gware da yin magana da hausa ba ita dai Hayat da ido kawai ta ke bin su ta kassa cewa komai zuciyar ta sai duka uku uku ta ke yi ta na rokon Allah ya sa ba irin su Hajiyah ne ba a hankali Nihal ta kai hannu ta dauki barin Apple guda ta kai bakin Hayat ta na fadin " bude baki " ba musu Hayat ta bude baki a hankali Nihal ta saka mata Apple din nan Vedad na ganin haka ya saki dan karamin kukan shagwaba har da bubuga kafafun shi a kassa da sauri duk mutanan wajen su ka kale shi , har Iqbal da Ummi su na hada baki su na tambayar shi lafya cike da shagwaba ya ke musu " Why mummy za ta ba ta a baki , ni wlh ba na so " dan karamin murmushi Nihal ta yi sannan ta ce " Haba my angel ba ka ga ba ta da lafiya ne " " uhm uhm ni ki daina ba ta a baki ta sa hannun ta , ni kadai za ki dinga ba wa a baki , ni na ma tafi na fadawa big bro " Vedad ya fada ya na turo dan bakin nan na shi kafin ya tashi ya nufi stair ya Haye da kallo duka su ka raka shi har sai da ya Haye sannan Nihal da Ummi su ka yi yar karamar dariya Nihal ta kai hannu ta dauki wani Apple din ta kai wa Hayat a baki ta na fadin " rabu da shi ci abin ki , Ba ki dai jin wani ciwon a jikin ki ? " a hankali Hayat ta gyada mata kai allamun eh Iqbal da ke bayan ta ne ya ce " Ki saki jikin ki kin ji , ba abun da zai faru da ke " cike da zolaya Ummi ta ce " ko dan kin gan mu jajaye ba mu yi kama da Hausawa ba " ta kai karshen ta na daga mata gera guda yar karamar dariya Hayat ta yi murya kassa kassa ta ce " Haske ne kawai gare ku amma da ga gani an san jinin hausawa ne ku " " Ashe dai ba kurma ba ce " Iqbal ya fada ya na yar dariya dariya ita ma Nihal ta yi kafin ta ce " Kai ya isa haka , ku bar ta , ta sha fruits din ta da ga baya kun yi magana " Shiru su ka yi ba wanda ya sake cewa komai su na kallon Hayat sannu sannu har ta fara sakin jiki ta na karbar Fruits din da Nihal ke ba ta su na a haka daya da ga cikin Chef ya fito da ga dining room ya na rike da tray dauke da wani plate an rufe shi da wani , da glass biyu daya na ruwa daya na juice a haka ya karaso cikin parlourn ya ajiye tray din saman table gaban Su Nihal sannan ya juya ya koma inda ya fito ya na barin wajen Nihal ta kai hannu ta bude plate din shake ya ke da jollof rice ta sha vegetable da fried chicken sai tashin kamshi ta ke har yawu na sai da ya tsinke kamar na kai hannu na debo a hankali Nihal ta kai hannu ta dauko plate din ta dauki Spoon ta debo ta kai bakin Hayat ta na fadin ta bude baki ba musu Hayat ta bude baki ta karba , dama ta na daura ido saman abincin ya shiga ran ta , sannu sannu har ta zame ta ci abinci har sai da ta ciye duka sai da ta cinye sannan Nihal ta ajiye Plate din saman tray sannan ta dauki glass din ruwa ta kai mata a baki ba musu ta bude baki ta shanye ruwan tass sannan ta sauko da glass din ajiye shi saman tray Nihal ta yi sannan ta dauki na juice ta mika mata ta na fadin " yanzu tun da cikin ya cika an samu bakin magana ko ? " a hankali Hayat ta gyada mata kai ta na wani dan karamin murmushi ita ma Nihal murmushi ta yi kafin ta kali Iqbal ta ce "Iqbal meda tray din nan kitchen " da okay ya amsa mata kafin ya tashi ya dauki tray din biyu duka ya kai dining room ya ajiye saman dining table sannan ya yi wa door din kitchen knocking guda sannan ya juya ya dawo parlour ya zauna geffen Ummi ya na zama Nihal ta kali Hayat ta ce mata " yanzu fada min ya sunan ki kuma da ga ina kike " Dan sunkuyar da kai Hayat ta yi sannan ta ce mata " suna na Hayat , ni yar kassar Nijer ce , da ga kauyen NAWACH KALÉ da ke a zinder " da ga haka ta shiga ba su labarin abun da ya faru tun zancen auren ta da Rabeh yadda a ka yi ta tsere har ta shigo kano da hadu da Hajiyah ta kawo ta kaduna har zancen da su ka yi na sayar da ita har kona gidan da ta yi duk ba ta boye musu har lokacin da ta fado gaban motar Su sumar zaune duk mutanan wajen su ka yi , yanzu da iya shekarun nan na ta har za ta iya kashe mutun " ki yi hakuri , amma fa nan gidan sojawa ne ki ka fado , dole mu hukun ta ki , kin yi kokarin kashe har mutun biyu , wa ya sani yanzu ko sun mutu , bari ma na kira yan sanda su fido mota mu tafi da ke " Iqbal ya fada cike da zolaya A razane Hayat ta saki glass din hannun ta ya fadi kassa nan take idanun ta su ka kawo ruwa ta shiga girgiza mishi kai ta na fadin " a'a don Allah ku yi hakuri ni babu inda zan je , ba zan je gidan yari ba , don Allah kar ku kira yan sanda " ta kai karshen kuka na kubce mata da sauri Nihal ta rungumota ta na fadin " kontar da hankalin ki wassa ya ke miki , da ga nan gidan ku za ki koma , babu inda za ki je kin ji ko ? " Bushewa da dariya Iqbal ya yi har da dafe ciki hannu Ummi ta kai ta buge shi ta na fadin " ka ji dadi ko , ka saka ta kuka " cikin dariyar ta shi ya ce " shikenan , i'm sorry wassa ne fa na ke mata " ya na gama fadar haka ya taso ya tsaya gaban Hayat ya dan sunkuyar da kai ya na fadin " Yi hakuri kin ji wassa na ke miki " ya na gama fadar haka ya nufi stair ya Haye ya na ci gaba da dariyar shi MY BOOK IS ONLY ₦300 VIA 8081129487 Khadija Sabi'u Monie point bank KU TURA SHAIDAR BIYAN TA WANNAN NUMBER +22795577612 or +22798999753 TAღRIN ZღCIYA 💖🌺💍 ( RETღRN ) (ROMANTIC LUV STORY )💋🔥 ❤👑 ꪑꪖꪶꪶꪖƙỉ᭢ ᩏꪹỉ᭢ᨶꫀకక ꪑꫀꫀꪹꪖꫝ 👑❤ 🕊💞 Wattpad : @bennybite Marubuciyar littafin TAURIN ZUCIYA EXILED PRINCE ( LOVE MEETS POWER ) TWO LIGHTS ( YAR JARIDA ) and now TAURIN ZUCIYA ( RETURN ) FOR MORE INFORMATION KU TABO WANNAN NUMBER +22798999753 WHATSAPP ONLY , Thanks 👍💕 اللَّهُمَّ صَلِّ عَلَى مُحَمَّدٍ وَعَلَى آلِ مُحَمَّدٍ، كَمَا صَلَّيْتَ عَلَى إِبْرَاهِيمَ وَعَلَى آلِ إِبْرَاهِيمَ، إِنَّكَ حَمِيدٌ مَجِيدٌ، اللَّهُمَّ بَارِكْ عَلَى مُحَمَّدٍ وَعَلَى آلِ مُحَمَّدٍ، كَمَا بَارَكْتَ عَلَى إِبْرَاهِيمَ وَعَلَى آلِ إِبْرَاهِيمَ، إِنَّكَ حَمِيدٌ مَجِيدٌ️ TAP THIS LINK TO JOIN MY WHATSAPP GROUP COMMETS SECTION 👇👇👇👇👇👇 https://chat.whatsapp.com/BoRRwG9bqUFBt4djqzcNbb DOMIN SAMUN BOOK DI NA DA GA FARKO ZA KU IYA ADDING CHANEL DI NA TA WANNAN LINK 👇👇👇👇👇👇 https://whatsapp.com/channel/0029VaGhJCqKmCPUvpvIJ80i 𝗧𝗔𝗣 𝗧𝗛𝗜𝗦 𝗟𝗜𝗞𝗘 𝗧𝗢 𝗝𝗢𝗜𝗡 𝗠𝗬 𝗣𝗢𝗦𝗧𝗜𝗡𝗚 𝗥𝗢𝗢𝗠 👇👇👇👇👇👇👇 https://chat.whatsapp.com/LWmuu0yv6C9DAhpdepDb4i _________________✦✦✦✦✦✦✦✦✦✦✦✦✦✦✦__________________ PAGE ............12.........❤🥂 sai da ya Haye stair sannan Nihal ta dago Hayat da ga jikin ta ta ce mata " yi hakuri kin ji ko ? babu inda za ki je , Ummi ! tashi ki kai ta bedroom din ta , ki gwada mata yadda za ta yi aiki da toilet , ta yi wanka , na san cikin kayan ki ba za a rasa kanana ba , ki ba ta ta saka , yanzu ina yi mata online shopping , da ta samu sauki mu maida ta gidan su " da to Ummi ta amsa mata kafin ta mike ta riko hannun Hayat ta mikar da ita tsaye sannan su ka nufi corridor su ka shiga part din Ummi ta shiga da ita dayan bedroom , su ka wuce toilet ta gwada mata yadda abubuwan su ke aiki , sannan ta cika mata bath da ruwa sannan ta fice toilet din ta bar bedroom din ta shiga na ta ▪NIHAL 🥀 Ummi ta na barin wajen Vedad ya sauko da ga stair a hankali ya na kuka kamar baby Da kallo Nihal ta rako shi har sai da ya karaso cikin parlourn ya nufi sofar ta ya Haye ya konta ya tada kan shi da cinyar ta a hankali ta daura hannun ta kan shi ta fara shafa wannan lalawsan gashin kan shi ta na fadin " wa ya taba min my angel , ba dai Iqbal ya buge ka " cikin kukan na shi ya ce " Mummy big bro ne , tun dazu da na hau bedroom din shi ta na rufe na yi ta jiran shi har kiran shi na dinga yi amma ya kyale ni " " oh ni Nihal ! " ta fada cikin zuciyar ta a fili kuma ta ce " haba my angel , may be ya yi kwana , yanzu tashi ka taya ni yi wa Hayat online shopping " a hankali ya dago kan shi ya na mikewa zaune kamar ba shi ne ba yanzu ke kuka ya ce " amma mummy ni zan zabar mata duka " dan karamin murmushi Nihal ta yi ta na fadin " shikenan yadda ka ke so haka za a yi " ta kai karshen ta na daukar wayar ta da ke geffen ta saman sofar sannan su ka shiga yi wa Hayat online shopping , kayan da su ka saya mata ko wata amaryar ba za ta same su ba , kamar wadda a ke shirya wa kayan lefe , ba abun da ba su sayo mata ba har underwear da takalmi har da su sneakers duk aikin Vedad ne , duk abun da ya gani sai ya saya har kananan kaya bai bari ba a takaice sai da su ka kashe wajen one million of dollars ba ma naira ba sai wajen karfe 10 na dare sannan su ka tashi , Vedad ya koma bedroom din shi , Nihal kuma ta nufi bedroom din ta ita ma ▪HAYAT 💦 Bayan Ummi ta fita toilet din ta rufe mata kofa , ta shiga yin wankan ta cikin nitsuwa ta yi wankan ta , sannan ta dauro towel a kirjin ta ta fito Toilet din Ta na fitowa ta ga wasu kananan kayan barci shanye saman gadon a hankali ta nufi kayan ta kai hannu ta dauke su , ko underwear ba ta saka ba , ta saka kayan barcin sannan ta Haye saman gadon ta na Hayewa Ummi ta turo kofar ta na sallama a hankali Hayat ta juyo kan ta , ta kali kofar ta na amsa mata ta karaso cikin dakin Ummi ta yi ta zauna bakin gado ta mikawa Hayat gorar ruwan da ke hannun ta ba musu Hayat ta kai hannu ta karba ta na karba Ummi ta mika mata wasu drugs a hannun ta ta na fadin " karba ki sha magani ne zai sa ciwon ki ya warke da sauri " a hankali Hayat ta gyada mata kai ta kai hannu ta ta karbi durgs din ta kai a baki sannan ta kai gorar ruwa a baki dama Ummi ta cire murfin ta shanye maganin sannan ta sauko gorar ruwan ta mikawa Ummi karba Ummi ta yi ta ajiye saman bedside drawer sannan ta juyo da kyau ta kali Hayat ta ce " yanzu fada min shekarun ki nawa ? " Dan karamin murmushi Hayat ta yi kafin ta ce " 14 " a takaice " wow , kin san fa na yi ɗiya da ke , ni na kusa cika shekara 30 , da a ce na yi aure a shekara 16 , da yanzu ina da daughter dai'dai ke " dan karamin murmushi Hayat ta yi kafin ta ce " Inna ta 33 gare ta " " ki ce yarinya ce kamar ni " Ummi ta fada cike da zolaya dariya sosai Hayat ta yi , cikin dariyar ta ta ke fadin " Yanzu ke ce yarinyar , Tab kenan har yanzu ni jaririya ce , Yanzu yaran ki nawa " girgiza mata kai Ummi ta yi ta na fadin " ko daya , ko saurayi ban taba yi bare aure " " laaa a shekarun ki , kuma ba ki da aure Tab , kin ji dadin ki gaskiya " " Haka ki ke gani ? " Ummi ta fada ta na daga mata gera guda cike da zamudi Hayat ta ce mata " eh mana kin ga ba wanda ke ce miki ki yi abu kaza , ki daina wannan abun , babu wanda za ki kula da shi sai kan ki , Ki ci abin da ki ke so , ki sha abin da ki ke so , ki saka abin da ki ke so , Ki na rayuwar ki cikin konciyar hankali , Ko ni da zan samu irin wannan damar , sai na zagaye duniya baki daya ina sha'ani na " ta fada ta yar karamar har da ware mata hanayan ta Dariya sosai Ummi ta yi , dan maganar ba karamar dariya ta ba ta ba ganin yadda Ummi ke wannan dariyar ne ya sa Hayat yin shiru ta koma ta na sunkuyar da kan ta ta ce " ki yi hakuri " " no kar ki damu , Ina jin dadin ganin ki ki na dariya ba karamin kyau ki ke yi ba , gaskiya bari na yi wa mummy magana ta yi wa General kamu " Ummi ta fada ta na kai hannu ta ja kumatun Hayat " uhm uhm ni gaskia ban shirya aure ba har yanzu ni jaririya ce , kuma ni ban ma san wanda ki ke cewa , kuma , kuma inna ta ba...... " cikin nitsuwa Ummi ta katse ta da cewa " kontar da hankalin ki babu wanda zai yi miki auren dole , ke da kan ki idan ki ga General za ki ji ki na son kasance wa tare da shi , Kin ga ai ina da kyau ko " a hankali Hayat ta gyada mata kai allamun eh " to yadda na ke haka shi ma General ya ke , saboda Tawaye na ne , ya na da kirki sosai , sai dai ba ya son raini , idan ka ce za ka raina shi , zai yi wa mutum dukan mutuwa , kuma ba izinin ramawa , shi fa bai taba kallon mace ba ya ce ya na son ta , matan ke biyar shi , su na cewa su na son shi , bai cika yawwan magana , kin ga tun zuwan mu Nigeria ko so guda bai sauko da ga dakin shi ya zo ya zauna tare da mu , ya yi hira , kullum ya na cikin dakin shi , sai dai me son magana da shi ya tarda shi dakin shi , mutum ne shi da ba ya son hayaniya sam " " To ni na minene za ki fada min wannan abun dukka ? " Hayat ta fada dan ba ta gane inda Ummi ta nufa wani cool murmushi Ummi ta yi kafin ta ce " ina son ki zama matar sa , ban san dalilin da ya sa na ke jin mugun son ki raina kamar yarinyar da na haifa , Dan uwa na mutum ne me kirki da kyakyawar zuciya , Ya kamata a ce ya samu matar da za ta kula da shi a yanzu , wadda za ta kontar mishi da hankali , dan kullum cikin damuwa ya ke , rabon da na dan uwa na ya yi ko dan karamin murmushi yanzu an yi shekara 20 , bayan ni da mummy , babu mace a cikin gidan nan , lokaci guda na ji dadin zama da ke a gidan nan kuma gaskia ba na son ki tafi ki bar mu " dan karamin murmushi Hayat ta yi kafin ta ce " da ga gani ki na son dan uwan ki " gyada mata kai Ummi ta yi ta na fadin " sosai ma , ina son shi fiye da komai na wa , shi kadai na ke kallo na ji dadi cikin zuciya ta , ina son ya ji wannan dadin cikin zuciyar shi shi ma , ba ki san irin abubuwan da ya yi na al'hairi a rayuwar shi , kullum cikin yi mishi adu'a da Fatan Al'hairi mutane ke yi mishi , shi ya sa na ga ya dace a ce yanzu ya na da na shi familyn " " to ke me ya hana ki yin auren kema , na ga ai shekarun ki daya " girgiza mata kai Ummi ta yi kafin ta ce " ki yi hakuri ba zan iya fada miki ba , yanzu dai konta ki huta nan da kwana biyu idan kin samu sauki za mu meda ki gidan ku " ta kai karshen ta na mikewa , ta riko kafadun Hayat ta kontar da ita sannan ta janyo duvet ta rufe ta har zuwa kirji sannan ta ce mata sai da safe , da ga haka ta kai sannu ta kashe lamps din dakin ta kunna bedside lamps , sannan ta fice dakin ta koma na ta Ummi na fitowa ta ci karo da Nihal zaune saman sofa kallon ta da kyau Ummi ta yi kafin ta karaso geffen ta ta zauna ta na fadin " Mummy kin jima a nan ne " abun da ba ta sani ba tun lokacin da su ka fara maganar nan da Hayat Nihal ta shigo dakin , dama ta zo ta duba in Ummi ta ba ta maganin ta shi ne ta jiyo su su na magana , duk hirar nan da su Ummi su ka yi Nihal ta ji su dan karamin murmushi ta yi kafin ta ce " ban jima ba yanzu na shigo " " okay ni zan shiga na konta " Ummi ta fada ta na kokarin mikewa da sauri Nihal ta ce mata " zauna ina son mu yi wata magana " ba tare da ta zauna ba ta ce " mummy in dai maganar aure na ce to ki bar ta kawai sai da safe " ta fada ta na fara takawa ko taku biyu ba ta yi ba Nihal ta riko hannun ta ta ce " no ba maganar auren ki ba ce , maganar auren Ash ce , ina son na ji ra'ayin ki a kai , ina son na nema mishi auren yarinyar nan Hayat " da sauri Ummi ta dawo ta zauna geffen Nihal ta na washe baki ta ce " kin ga ko mummy ni ma maganar nan ta na cikin rai na sosai , Yarinyar nan za ta dace da General " hararrar wassa Nihal ta yi mata ta na fadin " to sannu madam , to ke yaushe za ki samu wanda zai dace da ke , kar ki manta ce min ki ka yi duk ranar da Ash ya yi aure ke ma za ki yi , to ki shirya ki fido da mijin aure dan Ash ya samu mata " yar karamar dariya Ummi ta yi kafin ta ce " mummy kar ki damu in har General ya yi ni ma zan yi in sha Allah " " to na ji shikenan , yanzu ya ki ke so mu yi ? " " nothing , kawai mu bari yarinyar nan ta kwana biyu tare da mu , mu ga yanayin ta , mu ga halayan ta , mu koya mata wasu abubuwa da ga baya sai mu meda ta gidan su , da ga nan a nema mishi auren ta , idan iyayen ta sun yarda , sai a yi auren nan wajen ki dawo da ita mu koya mata yadda za zauna da shi , abun da ya ke so , abun ba ya so da ga nan sai mu sakawa ikon Allah ido " " shikenan to yadda ki ka ce haka za a yi " ta na gama fadar haka ta tashi ta nufi kofar fita da kallo Ummi ta raka ta har sai da ta fita sannan ta tashi ta shiga bedroom din ta ita ma ( MISALIN KARFE 12 NA DARE ) ▪ASH 🔥 A hankali ya sauke wata nanauyar ajiyar zuciya ya na juyawa ya koma saman bayan shi slowly ya fara ware idanun shi ya na fuskantar ceiling , sun koma Farare kal kamar da farko mike hanayan shi ya yi ya na yar mika da allamun barcin ya yi mishi dadi sai da ya dauki wajen good ten minutes a haka kafin ya sauko da kafafun shi kassa ya mike zaune da ga haka ya mike tsaye ya nufi Toilet ko rufe kofar bai yi ba After some minutes ya fito sanye da bathrobe ya wuce kai tsaye dressing room jim kadan ya fito sanye da kayan barcin shi farare kal , ya saki wani wannan black curly hair din na shi , sai tashin kamshi ya ke yi wajen bedside drawer ya nufa ya dauki wayar shi ya saka cikin aljihu sannan ya nufi kofar fita dakin ya daura hannun shi saman finger print , nan take kofar ta saki wata yar karamar kara sannan ta yo baya ta bude kan ta ta na budewa ya sa kafa ya fito parlour , nan ya ga tray din fruits da junior da ya ajiye mishi doguwar sofar ya nufa ya zauna , sannan ya kai hannu ya matso da table din ya fara shan Fruits din , dan tun jiya rabon shi da ya wani abu a bakin shi , shi dama ba wani ma'abocin ciye² ba ne ko rabin fruits din bai sha ya tashi ya dauki tray din ya fito part din , kai tsaye stair ya sauko ya nufi dining room ya ajiye tray din saman dining table , sannan ya juya ya nufi parlour ya zauna ya kai hannu cikin aljihun shi ya ciro wayar shi , ya sunkuyar da kai ya fara latsawa nan take duk jelar shi ta zubo mishi ta rufe mishi fuska , sam bai damu ba ya ci gaba da aikin shi bai yi one minute ba da zama wani jibgegen soja ya shigo parlourn , Sai da ya nufi Ash ya sara mishi sannan ya nufi stair ya Haye ▪HAYAT 💦 A hankali ta fara kokarin bude idanun ta ta na karanto adu'ar tashi da ga barci ware idanun ta ta yi ta na fuskantar ceiling , a hankali ta kai hannun saman cikin ta , kafin ta sauko da kafafun ta kassa ta mike zaune sannan ta mike tsaye ta nufi kofar fita , ta fito parlour a hankali ta fara bin parlourn da kallo , cen ta hango wata yar karamar fridge kusan Kofar bedroom din Ummi da sauri ta nufi Fridge din nan , ta kai hannu ta bude a tunanin ta za ta samu wani abu sai dai ba komai ciki da ga ruwa sai juice dan karamin tsaki Hayat ta yi kamar ta yi kuka ta ce " ya zan yi ni yanzu yunwa na ke ji " a hankali ta juya ta kali kofar fita part din sannan ta juyo ta kali kofar dakin Ummi , cije lips din ta na kassa ta yi sannan ta juya ta nufi kofar fita part din a hankali ta ke tafiya cikin corridor din kamar barauniya a haka har ta fito ta nufi dining room , ta na zuwa ta ga tray din Fruits saman dining table dan karamin murmushi ta saki kafin ta nufi dining table din ta janyo chair guda ta zauna ta janyo tray din gaban ta , ta fara shan Fruits din cikin konciyar hankali sai da ta ji ta koshi cikin ta ya cika sannan ta mike ta meda chair din wajen ta sannan ta juya za ta koma cikin corridor din idanun ta su ka sauka saman shi ya na nan zaune ko motsawa bai yi ba ya na faman latsa wayar shi , tun fitowar ta da ga cikin corridor ya jiyo ta amma bai dago kan shi ba , asali ma a tunanin shi Ummi ce , shi ya sa bai dago kai ba tsare shi da idanu Hayat ta yi cikin zuciyar ta ta na fadin " Aunty fa ce min ta yi su biyu ne mata cikin gidan , wagga kuma fa " dan zaro idanu ta yi murya kassa kassa ya ce " kar a je aljana ce , dan wannan jikin ta bai yi kama da na mace ba " ta na gama fadar haka ta nufi corridor da gudu ta shige ta nufi part din Ummi ta shige bedroom din ta , ta Haye saman gadon ta janyo bargo ta rufe har kan ta , ta na karanto ayatul kursi kar a je aljana ce ta gani , ga ta zaune tsakiyar parlour tsakar dare babu me rai ita kadai , ga yanayin jikin ta sam bai yi kama da na mace ba , ita gashin nan da ta gani ya sa ta tunanin mace ce , sam ba ta lura da murdaden jikin shi Ash kuma ya na jin ta shige corridor ya dago kan shi a hankali ya kali Saitin corridor din wani dogon nunfashi ya ja kafin ya yi baya ya jingina bayan shi a jikin sofar ya lumshe idanun shi murya cen kassan makoshi kamar mai rada ya ce " I really miss you Dad " ya na gama fadar haka wannan sojan ya sauko da ga stair , wannan karan ma sai da ya nufi Ash ya sara mishi sannan ya nufi kofar fita parlourn ya fice Slowly Ash bude idanun shi sannan ya tashi ya nufi stair ya Haye ya koma part din shi ya na shiga wani dadaden kamshi ya kai mishi karo , a haka ya karaso ya nufi bedroom din shi a hankali ya bude kofar ya shiga , wani mugun sanyi mai dadi dakin ya ke , an gyara komai na cikin dakin , an sauya bedsheet , da Duvet din , an saka wasu ma su launin Sky blue , sai mugun kamshi su ke yi , da allamun dai sojan nan gyaran part din ya hayo ya shigowa ya nufi bed din shi , ya zauna bakin gadon ya kai hannu ya ajiye wayar shi saman bedside drawer sannan ya kashe lamps din dakin duka har da bedside lamps , sannan ya sa hannu ya cire rigar jikin shi ya tila ta saman sofa , ya ida Hayewa bed din ya konta ya janyo duvet ya rufe jikin shi har zuwa kirji sannan ya daura hannun shi saman forehead ya lumshe idanun shi , a hankali ya fara karanto adu'ar barci , da ga haka wani nanauyan barci ya dauke shi , asuba ta gari ▪WASHE GARI ( Misalin karfe 8 ) a hankali lips din shi ke motsi ya na karanto adu'ar tashi da ga barci , kafin ya ware idanun shi ya na fuskantar ceiling a hankali ya fara jiyo Muryar Vedad cike da nitsuwa ya na wata yar waka slowly Ash ya juyar da kan shi , nan ya ga Vedad zaune saman bed din ya jingina bayan shi a jikin forehead din gadon , ya na rike da wayar shi ya na latsa wa , ya na motsa lips din shi a hankali ya na fadin " MIRRORS , THEY NEVER LIE DON'T SEE MYSELF INSIDE WHY CAN'T I GET IT RIGHT ? I DON'T KNOW ! YOU'RE ALWAYS WATCHING ME FALL SHADOW THEY LIKE MY WALL WHY DO I FEEL SO SMALL ? I DON'T KNOW SO , I WALK INTO THE DEAD OF NIGHT WHERE MY MONSTERS LIKE TO HIDE CHAOS FEELS , SO GOOD INSIDE NOW I KNOW I LOST , I LOST , I LOST CONTROL AGAIN ALWAYS DO THE SAME AND I'M TO BLAME I LOST CONTROL AGAIN I DON'T , I DON'T , I DON'T KNOW WHO I AM ALWAYS DO THE SAME AND I'M TO BLAME I LOST CONTROL AGAIN " a hankali Ash ya dago hannun shi ya daura saman laps din Vedad a razane Vedad ya daina wakar shi ya juyo ya kali Ash wani dan karamin murmushi Vedad ya saki ya na fadin " Good morning Big bro " dan lumshe idanun shi Ash ya yi kafin ya sake bude su a hankali ya ce " ka ji dadi ka tashe ni ko " a hankali Vedad ya girgiza mishi kai ya na turo dan bakin nan na shi cikin shagwaba ya ce " no ni ban tashe ka ba , ka ga ma tafiya ta " ya na gama fadar haka ya ajiye wayar Ash saman bedside drawer ya sauko da ga saman gadon ya nufi door ya ficewar shi shi dai Ash da kallo kawai ya raka shi har sai da ya fita sannan ya kai hannu ya dauki wata remote saman bedside drawer ya danna wasu button , nan take kofar dakin ta meda kan ta , ya saka mata security , sannan ya kashe lamps din dakin sannan ya meda remote din saman bedside drawer , ya kai hannu ida janyo duvet din shi har kai ya rufe jikin shi ya ci gaba da barcin shi , da allamun kwana biyun nan General na samun hutu ▪HAYAT 💦 konce ta ke tsakiyar Gadon ta , ta na kallon ceiling , tun wajen karfe 6 ta farka da ga barcin ta , amma ta kassa motsi kawai ta tsaya ta na kallon ceiling din ta na a haka Ummi ta turo kofar dakin ta shigo ta na sallama a hankali Hayat ta juyo kan ta ta kali saitin kofar ta na amsa mata sallamar , sannan ta mike zaune ta na fadin " Ina kwana Aunty " cike da fara'a Ummi ta amsa mata gaisuwar ta sannan ta ce " na ɗauka har yanzu ba ki tashi ba " dan sunkuyar da kai Hayat ta yi ta na murmushi ba ta ce komai ba dan karamin murmushi Ummi ta yi kafin ta ce " Shikenan yanzu tashi mu tafi ki yi wanka , Zuwa gobe kayan ki za su iso " cike da rudu Hayat ta ce " Wane kaya Aunty ? " " kar ki damu , yanzu tashi mu je ki yi wanka " " Aunty ba sai kin raka ni , na iya wanka " Hayat ta fada ta na saukowa da ga saman gadon yar karamar dariya Ummi ta yi kafin ta ce " kar ki damu , zan gwada miki yadda a ke yin brush , na kuma wanke miki gashin kan ki , sai ki yi wankan ki " murmushi kadan Hayat ta yi ta na gyada mata kai sannan ta nufi toilet , Ummi na biye da bayan ta , su ka shiga toilet din tare ▪AFTER SOME MINUTES Sai da su ka dauki wajen good one hour a cikin toilet din , har wanka sai da Ummi ta yi wa Hayat kun san fa turawan nan ba kunya su ka sani ba , Ita Ummi ko a jikin ta , ta yi wa Hayat Wanka da kyau ta gwada mata yadda a ke yin brush , ta wanke ma ta gashi , tubarikallah ta na da gashi sosai har tsakiyar bayan ta , Baki da shi amma ya yi wani russet da ga tsakiya gwanin burgewa ga sulbi kuma bayan sun fito da ga cikin toilet din , Ummi ta zaunar da Hayat saman chair din gaban dressing mirror , ta je dakin ta ta dauko hairdryer ta bushe mata gashin ta , Ta daure mata shi a baya " bara na dauko miki kayan da za ki saka " Ummi ta fada ta na juyawa ta fice dakin ita dai Da ido kawai ta ke bin Ummi , sai da ta fita sannan Ta kali mirror din gaban ta kamar ba ita ba , har wani haske ta kara , ta kara kyau , color din nan na chocolate ya fito da kyau , kawai sai ta tsargu da kallon kan ta cikin mirror din babu ko kiftawa ta na a haka Ummi ta dawo cikin dakin ta na sallama ta na rike da wata gown Sky blue a haka ta karaso ta tsaya bayan Ummi ta mika mata Rigar ta ce " tashi ki shiga dressing room sai ki saka su , akwai pant amma banda Bra din da za ta miki shi ya sa na dauko miki Vest din nan " ta fada ta na mika mata kayan da to kawai Hayat ta amsa mata sannan ta mike da ga saman chair din nan ta karaso gaban Ummi ta kai hannu ta karbi kayan sannan ta juya ta shiga dressing room da kallo Ummi ta raka ta har sai da ta shiga sannan ta zauna bakin gadon sannu sannu har sai da Ummi ta share wajen ten minutes zaune bakin gadon Hayat ba ta fito ba a hankali ta juya ta kali kofar dressing room ta na fadin " kar a je ta kassa saka rigar " ta kai karshen ta na tashi ta nufi kofar dressing room ba ta yi taku biyu ba ta tsaya cak ta na kallon kofar dressing room a hankali Hayat ta bude kofar ta fito ta na sunkuyar da kai Allahuma barik , Baki na ya yi kadan ya fada muku irin kyawon da idanu na su ke gani , kamar a jikin ta a ka yi rigar nan , ta zauna mata dai'dai a jiki , Shape din ta sun fito gwanin burgewa rigar da kan ta abun kallo ce , da kadan ta wuce mata guyiwowi , ta na da dogayen hannu , ta sha Stone da ga tsakiya kamar belt gaskiya na kassa fada muku irin kyawon rigar da ma wadda ke sanye da rigar a hankali ta ke takowa ta karaso gaban Ummi ta tsaya sannan ta dago kan ta ta saki wani cool murmushi MY BOOK IS ONLY ₦300 VIA 8081129487 Khadija Sabi'u Monie point bank KU TURA SHAIDAR BIYAN TA WANNAN NUMBER +22795577612 or +22798999753 TAღRIN ZღCIYA 💖🌺💍 ( RETღRN ) (ROMANTIC LUV STORY )💋🔥 ❤👑 ꪑꪖꪶꪶꪖƙỉ᭢ ᩏꪹỉ᭢ᨶꫀకక ꪑꫀꫀꪹꪖꫝ 👑❤ 🕊💞 Wattpad : @bennybite Marubuciyar littafin TAURIN ZUCIYA EXILED PRINCE ( LOVE MEETS POWER ) TWO LIGHTS ( YAR JARIDA ) and now TAURIN ZUCIYA ( RETURN ) FOR MORE INFORMATION KU TABO WANNAN NUMBER +22798999753 WHATSAPP ONLY , Thanks 👍💕 اللَّهُمَّ صَلِّ عَلَى مُحَمَّدٍ وَعَلَى آلِ مُحَمَّدٍ، كَمَا صَلَّيْتَ عَلَى إِبْرَاهِيمَ وَعَلَى آلِ إِبْرَاهِيمَ، إِنَّكَ حَمِيدٌ مَجِيدٌ، اللَّهُمَّ بَارِكْ عَلَى مُحَمَّدٍ وَعَلَى آلِ مُحَمَّدٍ، كَمَا بَارَكْتَ عَلَى إِبْرَاهِيمَ وَعَلَى آلِ إِبْرَاهِيمَ، إِنَّكَ حَمِيدٌ مَجِيدٌ️ DOMIN SAMUN BOOK DI NA DA GA FARKO ZA KU IYA ADDING CHANEL DI NA TA WANNAN LINK 👇👇👇👇👇👇 https://whatsapp.com/channel/0029VaGhJCqKmCPUvpvIJ80i TAP THIS LINK TO JOIN MY WHATSAPP GROUP COMMETS SECTION 👇👇👇👇👇👇 https://chat.whatsapp.com/BoRRwG9bqUFBt4djqzcNbb 𝗧𝗔𝗣 𝗧𝗛𝗜𝗦 𝗟𝗜𝗞𝗘 𝗧𝗢 𝗝𝗢𝗜𝗡 𝗠𝗬 𝗣𝗢𝗦𝗧𝗜𝗡𝗚 𝗥𝗢𝗢𝗠 👇👇👇👇👇👇👇 https://chat.whatsapp.com/LWmuu0yv6C9DAhpdepDb4i _________________✦✦✦✦✦✦✦✦✦✦✦✦✦✦✦__________________ PAGE ............13.........❤🥂 Baki sake Ummi ke kallon ta , ba karamin kyau ta yi mata ba , kamar ta sace ta ta gudu " la la la , wacece wanan , ina Hayat di ta ta shiga " Ummi ta fada cike da zolaya murmushi mai dan sauti Hayat ta yi kafin ta ce " Aunty , ni ce fa , ba ki gane ni ba " " Masha Allah , Mu je mu yi breakfast to na San ki na jin yunwa " Ummi ta fada ta na kamo hannun Hayat su ka fice dakin a tare su ka fito part din kai tsaye su ka nufi parlour duk mutanan gidan su na nan zaune Banda Ash da ke part din shi , har junior ya na nan zaune su na hirar su Vedad na aikin da ya saba na zuba musu shagwaba su na a haka Ummi da Hayat su ka fito shigo parlourn Ummi na sallama a tare duk mutanan wajen su ka kai kallon su kan Ummi su na amsa mata sallamar ta su na sauke idanu kan Hayat amsar ta makale ta kassa fitowa , kowa ya tsare Hayat da ido baki sake Hayat kuwa duk ta bi ta tsargu , ta takure waje guda saboda irin wannan kallon da su ke yi mata su na a haka ta jiyo Muryar Junior ya na fadin " mummy wacece wanan kuma ? " Nihal na shirin magana Vedad ya riga ta cewa " Marshal ba ka gane ta ba , yarinyar da Iqbal ya buge ce jiya " ya kai karshen ya na mikewa tsaye ya nufo in da su Ummi ke tsaye ya kai hannu ya kamo hannun Hayat ya na fadin " mu je ki yi breakfast " da ga haka ya juya su ka nufi dining room , ya janyo mata chair da kan shi ta zauna shi ma ja ta geffen ta ya zauna ya kai hannu ya dauko plate din Pancakes da ke gaban shi ya kawo gaban ta ya na fadin " ke na ajiye wa , ci ya na da dadi sosai " ya na gama fadar haka ya jiyo Muryar Iqbal ya na fadin " yanzu Vedad na ce ka ba ni Pancakes din nan ka hana ! " " eh na hana ai ba kai na ajiye wa ba " Vedad ya fada cikin shagwaba ya na murguna mishi baki sannan ya kali Hayat da ta tsare shi da ido ya ce " Ki ci abin ki tun Iqbal bai saka miki ido ba " ya kai karshen ya na daukar fork ya mika mata ba musu ta karba ta tsaya ta na kallon Pancakes din ta ma rasa ta ina za ta fara ita ba ta ma san ko minene ba ta na a haka kawai sai ji ta yi Vedad ya kwace fork din hannun ta ya na fadin " bari na ba ki a baki " ya fada ya na kokarin yanko Pancakes din ya kai mata a baki ba musu ba bude baki ta karba a hankali ta fara taunawa daga mata gera guda ya yi ya na fadin " akwai dadi ? " da sauri ta gyada mishi kai allamun eh yar karamar dariya Vedad ya yi ya na ci gaba da ba ta a baki Nihal kuwa sai kallon su ta ke ta na murmushi , Allah kadai ya san abun da ta ke tunani dan idanun ta sun ciko da ruwa kallon Iqbal Ummi ta yi ta na fadin " kai Iqbal , wai ina General ya yi , tun jiya rabo na da shi " daga kafadun shi Iqbal ya yi allamun ban sani dan shi rabon shi da Ash tun shekaran jiya ba ma jiya ba " Ummi tashi ki dibo shi , ina ga ba shi da lafiya " Nihal ta fada ta na kallon Ummi gyada mata kai Ummi ta yi kafin ta tashi ta nufi stair ta Haye kai tsaye part din Ash ta nufa , da sallama a bakin ta ta shigo parlourn shi , ta ga babu kowa a ciki , sai ta wuce bedroom din shi har ta tura kofar a tunanin ta bude ta ke sai ta ga akasin hakan a hankali ta sa hannu ta fara yi mishi Knocking ta na fadin " General Bude Kofar nan Ummi ce " shiru ba a bude mata kofar ba , haka ta tsaya ta na ta bubuga ta ▪'ASH 🔥 tun bugun farkon da ta yi ya juyo ta amma ya kyale ta sai da ta yi wajen bugawa biyar sannan ya fido hannun shi da ga cikin duvet din , ya kai saman bedside drawer ya dauki remote ya danna wani button kofar dakin ta bude sannan ya saki remote din ya bar hannun nan saman bedside drawer kofar na budewa Ummi ta shigo dakin ta na yi mishi sallama nan ta gan shi konce saman gadon shi ya rufe duk jikin shi da duvet ga hannun shi nan saman bedside drawer a hankali ta karaso bakin gadon ta zauna , ta kai hannu ta kunna lamps din dakin sannan ta janye mishi duvet din nan idanun shi su na bude , ya kurewa waje guda ido har ta janye mishi duvet din shi bai motsa ba a hankali ta daura hannun ta saman neck din shi ta ji temperature din shi dai'dai ta ke " My Twins wai me ke damun ka ne , a sani na ba ka taba kai karfe 8 ka na kwana , yau har karfe goma ta yi ba ka motsa ba " ta fada cikin nuna damuwa a hankali ya motsa lips din shi ya ce mata " hutu na ke " ba ta san lokacin da wata yar karamar dariya ta kubce mata ba har ta daura hannun ta guda saman bayan shi ta na fadin " The General of American Army Staff Ash , yau da kan ka ke fadin hutu ka ke yi , fada min gaskia wane abu a ka yi " dan karamin tsaki Ash ya yi kafin ya sauko da kafafun shi kassa , ya mike tsaye bai ce mata komai ba ya fara takawa ya nufi toilet ya shiga ya bar ta nan After some minutes ya fito sanye da bathrobe , ta na nan inda ya bar ta , amma ta gyara mishi Bed din , ta na zaune a baki ta na rike da wayar ta bai ce mata komai ba ya nufi dressing mirror ya dauki lotion din shi ya fara shafawa sannan ya nufi dressing room ya shiga duk abun da ya ke ta na kallon shi ta kassan ido jim kadan ya fito sanye da Trouser Black color da T-shirt white color , kafafun shi kuma cikin wasu shagon sneakers farare kal ma su mugun kyau , ya saka wasu gloves bakake a hannayan shi , da wasu glass bakake a idanun shi , ya daure wanan lalawsan curly hair din na shi a baya sai tashin kamshi ya ke kamar companyn perfume abun dai Masha Allah amma dai fuskar nan a daure ta ke tamau kamar hadari , sam babu wassa a ciki ya na fitowa ya nufi bedside drawer ya dauki wayoyin shi , ko sannu bai ce ma Ummi ba ya nufi hanyar fita gidan da sauri Ummi ta riko hannun shi ta na fadin " General ina kuma za ka je ka kyale ni " slowly ya juyo ya kale ta cikin wadanan bakaken glass din shi cikin wata zazzakar sexy voice din shi ya ce mata " sake min hannu akwai wajen da za ni " yanayin da ya yi mata maganar ya sa ta sakin hannun shi babu shiri allamun yau mutanan sun hau , sam ba allamun wassa a tattare da shi yau ta na sakin hannun shi ya juya ya ci gaba da tafiyar shi da sauri ita ma ta mike ta bi bayan shi su ka fice part din tun da ya fara tako stair mutanan gidan su ka tsare shi da idanu , da Allamun yau na mulkin na sama bai bi ta kan su ya sa kai ya fice parlourn baki daya ya na fitowa duk sojojin da ke cikin gidan su ka tsaya cak waje guda su na daga kafa sama su na sara mishi amma bai bi ta kan su ya nufi wajen motar da a ka shirya mishi dan dama ya fada wa Felix ya shirya mota za su fita ya na isowa bakin motar Felix ya sara mishi ya na fadin " Good morning Sir " ya bude mishi kofar gidan baya bai bi ta kan gaisuwar shi ba ya shiga motar ya na shiga cikin motar Felix ya rufe ya zagayo da gudu ya shiga mazaunin driver ya tada motar , su ka bar gidan da mugun gudu sai da su ka bar gidan sannan sojojin nan su ka sauko da hannayan su , su ka ci gaba da aikin su , kawai dai su na ta zagaye gidan a cen cikin gidan kuma Ummi na sauko stair din ta ga Vedad da Hayat ba su cikin dining room , ba kuma su cikin parlour kallon Nihal ta yi ta na fadin " mummy ina kuma su Vedad su ka yi ? " " wai ya tafi ya gwada mata garden " Nihal ta fada ta na dan karamin murmushi mikewa Iqbal ya yi ya na fadin " bari na je na gani " ya kai karshen ya na fara takawa sofa Ummi ta nufa ta zauna ta na kallon junior ta ce " a'a Marshal ba tare za ku fita ba kenan ? " girgiza mata kai junior ya yi ya na murmushi kadan ya ce " no , shi ma ba zai jima ba yanzu ya dawo " ya fada ba tare da ya dago kan shi da ga saman wayar shi ba shiru ta yi ba ta ce mishi komai ba ta fara latsa wayar ta ita ma bangaran Iqbal kuma kai tsaye cikin corridor ya nufa , ya yi tafiya mai dan nisa kafin ya iso karshen shi wata door ce ta glass , ya na isowa ta zuge kan ta ya daga kafa ya shiga wani tanpasheshen garden ne , mai mugun girma , babu abun da babu a cikin shi akwai filin buga ball , da swimmig pool geffen filin cen karshen garden din ta ko ina cikin garden din ciyayi ne , da kananan flowers multicolore ma su mugun kyau , ko ina akwai kananan chair Farare irin na shan iska gefe guda kuma akwai wata Runfa mai dan girma an kawata ta da wasu lilo guda Uku ma su dan girma biyu na fuskantar juna , guda tsakanin su , da ga tsakiya kuma akwai wata table ta glass mai mugun kyau runfar duk zagaye ta ke da flowers gwanin burgewa cen ya hango Vedad da Hayat zaune saman lilo dan karamin murmush Iqbal ya yi kafin ya karaso wajen lilon ya na musu Sallama amsa mishi sallamar shi su ka yi sannan Vedad ya ce " yawwa gwara da ka zo , ce mata na yi dan uwa na Musician ne , amma ta ki yarda " hararrar shi Iqbal ya yi ya na fadin " yaushe na zama musician ban sani ba " ya kai karshen ya na zama saman lilon da ke fuskantar nasu juyowa Vedad ya yi ya kali Iqbal ya ce " Iqbal ka na tune da song din nan da Daddy je yawwan yi wa mummy ? " wani cool murmushi Iqbal ya saki kafin ya ce " yeah ina tune da shi " marairaice fuska Vedad ya yi kafin ya ce " please yi min shi " ya kai karshen kamar zai yi kuka gyada mishi kai Iqbal ya yi kafin ya dan jinkirta ya fara rero mishi waka ya na fadin " PICTURE PERFECT YOU DON'T NEED NO FILTER GEORGEOUS MAKE EM DROP DEAD YU'RE A KILLER SHOWER YOU WITH ALL MY ATTENTION , YEAH THESE ARE MY ONLY INTENTIONS STAY IN THE KITCHEN COOKING UP GOT YOUR OWN BREAD , HEART FULL OF EQUITY YOU'RE AN ASSET MAKE SURE THAT YOU DON'T NEED NO MENTIONS , YEAH THESE ARE MY ONLY INTENTIONS " ya na gama fadar haka ya yi shiru ya na kallon Vedad yar karamar dariya Vedad ya yi kafin ya ce " Your voice look like Daddy's voice , specially when you sing " cikin sanyin Hayat ta ce mishi " ni fa ban san abun da ku ke cewa ! " yar karamar dariya Vedad da Iqbal su ka yi a tare , sun ma manta da turanci su ke magana " sister , sai na koya miki turanci Gaskiya " Iqbal ya fada da hausa dan karamin murmushi Hayat ta yi kafin ta ce " Duk da ban san abun da ka ke cewa ba , Muryar ka na da dadin sauraro idan ka na waka " daga mata gera guda ya yi ya na fadin " Da gaske ki ke ? " a hankali ta gyada mishi kai ta na fadin " amma kai da gaske mawakin ne ko ? " wani cool murmushi Iqbal ya saki kafin ya girgiza mata kai ya ce " no , amma ya na daya da ga cikin abubuwan da su ke burge ni a rayuwa , kuma na rubuta wokoki na kaina har guda biyu , bari watarana zan rera miki su ki ji , Kafin nan zan koya miki turanci dan ki gane su " da sauri Vedad ya katse shi da cewa " amma ni kuma idan na ce ka min sai ka ki yarda " ya kai karshen cikin shagwaba yar karamar dariya Iqbal ya yi kafin ya ce " Don't worry My Cutie pie , zan yi maka very soon , bari ina yin order din Guitar online kafin mu koma US zan yi maka " wani kyawatencen murmushi Vedad ya saki ya na juyawa ya kali Hayat ▪NIHAL 🥀 zaune ta ke saman sofa , Ummi na geffen Junior kuma ya na Fuskantar su , duk su na rike da wayoyin su su na latsawa har Nihal su na a haka Ash ya shigo parlourn babu ko sallama ya nufi Stair a tare duk su ka dago kai jin takun mutum da sauri Nihal ta tseda shi da cewa " Ash , come here please " cak ya tsaya dai'dai ya daga kafa zai taka Stair na Farko Slowly ya janye kafar shi ya juya ya kali Nihal wani cool murmushi ta saki kafin ta ce " Ash , dawo ka zauna please ! " " Mummy yi maganar ki don Allah , Sauri na ke " " okay , za ka iya tafiya idan ka samu lokaci mun yi maganar " bai ce mata komai ba ya juya ya Haye Stair har ya kai tsakiyar Stair din ya ce ma Junior " Marshal , come with me " ya fada dai'dai lokacin da ya ida Hayewa Stair din ba musu Junior ya tashi ya Haye Stair din ya bi bayan Ash ya na ida Hayewa Ita ma Ummi ta mike ta ce wa Nihal " mummy ina zuwa " da ga haka ita ma ta nufi stair ta Haye Ash kuma kai tsaye part din shi ya nufa ya na isa ya zauna a parlour saman sofa ya fido wayar shi ya fara latsawa ya na a haka Junior ya shigo parlourn ya na sallama ya nufi sofar da Ash ke zaune ya zauna shi ma ya na kallon Ash ya ce " Ya ? ka kamo su ne ? ko kuma mun yi batan kai ? " ba tare da ya dago kai ba ya ce " No ! " a takaice cikin rudu Junior ya tambaye shi " ya kuma a ka yi ka dawo kai kadai ? " dan jinkirtawa Ash ya yi kafin ya ce " She is die " " Die ! How ? When ? wanene ya kashe ta " ajiye wayar shi Ash ya yi kafin ya juya ya kali junior ya ce " i don't know too , but duk wanda ya kashe ta ya kamata mu gano inda ya ke " " Wait , ta a ka yi ta mutu ma tukunna , ka ga gawar ta ne ? " a hankali Ash ya girgiza mishi kai kafin ya ce " babu wanda ya ga gawar ta saboda gidan ta baki daya su ka kona da ita a ciki , amma kuma mota biyu na gani cikin gidan kenan ba ita kadai ba ce akwai wani a tare da ita a lokacin " " Yanzu shikenan hanyar da ta rage mana mun rasa ta ? " " no ba mu rasa ta ba , yanzu dai mu fara kama wanda ya kashe ta , ta hanyar shi ne kadai za mu iya gano inda kungiyar ta ke " " okay , yanzu bari na duba CCTV din unguwar may be mu samu wani abu a kai " ya kai karshen ya na shirin tashi cikin nitsuwa Ash ya tseda shi da cewa " ko ka duba ba za ka komai ba , saboda tun jiya a ka kashe ta " slowly Junior ya koma ya zauna ya na tunanin wani abu kamar da ga saman su ka jiyo Muryar Ummi ta na fadin " ni na san wadda ya kashe ta " a tare Ash da junior su ka juya su ka kali Kofar dakin ta na tsaye ta na kallon su , tun farkon maganar su ashe ta na nan Tsaye ta na sauraron su a hankali ta karaso cikin dakin ta zauna saman sofa one seater ta na kallon Ash ta ce " General ina ga Matar da ku ke neman Hayat ta kashe ta " " who is Hayat ? " Ash ya fada cikin nitsuwa Ummi ta shiga ba shi labarin da Hayat ta ba su tun da ga Farko har kona gidan Hajiya da ta yi ba ta kai ga rufe bakin ta ba ta ga Ash ya ce mata ta kiro mishi yarinyar ya na son ya mata wasu tambayoyi ba musu Ummi ta tashi ta bar dakin ta na fita Ash ya mike shi ma ya shiga bedroom din shi After some minutes bai wuce five minutes ba Ummi ta dawo cikin dakin ta na rike da hannun Hayat sai ta ga Junior ne kadai zaune cikin parlourn " where is General " Ummi ta tambayeshi ba tare da ya ce komai ba ya nuna mata bedroom din Ash ta na rike da hannun Hayat ta nufi bedroom din ta tura kofar ta shiga ta na sallama sai dai babu Ash a ciki , Ita dai Hayat da ido kawai ta ke bin Ummi , da bedroom din dan tun da ta ke a duniya ba ta taba shigowa irin wannan Bedroom ba su na a haka Ash ya fito da ga cikin dressing kai a sunkuye ya na latsa wayar shi , ya karaso gaban gadon ya zauna ya na zama ba tare da ya dago kai ba ya ce " Ko za ki iya kawo min Fruits " da to Ummi ta amsa mishi kafin ta saki hannun Hayat ta juya ta fice ba tare da ta kawo komai a ran ta ba shi kuma ya na lure da ita har ta fice part din baki daya , sannan ya tashi a hankali ya raba ta geffen Hayat ya nufi door ta zata fita zai yi sai ta ga ya tura kofar ya rufe ta , ya juyo slowly ya dago kai " Inallillahi " ta fada cikin zuciyar dan ba karamin razana ta yi ba ganin wadanan sexy blue eyes din na shi a hankali ya tako ya tsaya gaban ta cikin sanyin murya ya ce mata " who are you ? " cike da tsoro ta ce mishi " ba na jin turanci " ta fada Muryar ta har kerma ta ke yi a hankali ya lumshe idanun shi kafin ya sake bude su slowly cikin zafin nama ya kai hannu ya damko wuyan ta ya shake ta ya na cewa " kar ki raina min hankali , su wanene su ka turo ki , kin zo ki kashe ni nima ko " wata razananiyar kara ce Hayat ta saki tare da kuka lokacin guda murya a shake ta ke cewa " ni ban san abun da ka ke cewa ba " wata gigitaciyar tsawa ya daka mata ya na cewa " shut up ! kar ki kuskura ki sake bude min wannan bakin naki , me ki ke yi a cikin gidan nan " ya fada da hausa wannan karan a hankali ta bude baki za ta yi magana ta kassa fitowa saboda shakar da ya yi mata a hankali ya fara ganin idanun ta sun koma jazir ta na lumshe su a hankali dan karamin tsaki ya ja kafin ya sake ta nan take ta sulale a kassa sumamiya MY BOOK IS ONLY ₦300 VIA 8081129487 Khadija Sabi'u Monie point bank KU TURA SHAIDAR BIYAN TA WANNAN NUMBER +22795577612 or +22798999753 TAღRIN ZღCIYA 💖🌺💍 ( RETღRN ) (ROMANTIC LUV STORY )💋🔥 ❤👑 ꪑꪖꪶꪶꪖƙỉ᭢ ᩏꪹỉ᭢ᨶꫀకక ꪑꫀꫀꪹꪖꫝ 👑❤ 🕊💞 Wattpad : @bennybite Marubuciyar littafin TAURIN ZUCIYA EXILED PRINCE ( LOVE MEETS POWER ) TWO LIGHTS ( YAR JARIDA ) and now TAURIN ZUCIYA ( RETURN ) FOR MORE INFORMATION KU TABO WANNAN NUMBER +22798999753 WHATSAPP ONLY , Thanks 👍💕 اللَّهُمَّ صَلِّ عَلَى مُحَمَّدٍ وَعَلَى آلِ مُحَمَّدٍ، كَمَا صَلَّيْتَ عَلَى إِبْرَاهِيمَ وَعَلَى آلِ إِبْرَاهِيمَ، إِنَّكَ حَمِيدٌ مَجِيدٌ، اللَّهُمَّ بَارِكْ عَلَى مُحَمَّدٍ وَعَلَى آلِ مُحَمَّدٍ، كَمَا بَارَكْتَ عَلَى إِبْرَاهِيمَ وَعَلَى آلِ إِبْرَاهِيمَ، إِنَّكَ حَمِيدٌ مَجِيدٌ️ DOMIN SAMUN BOOK DI NA DA GA FARKO ZA KU IYA ADDING CHANEL DI NA TA WANNAN LINK 👇👇👇👇👇👇 https://whatsapp.com/channel/0029VaGhJCqKmCPUvpvIJ80i TAP THIS LINK TO JOIN MY WHATSAPP GROUP COMMETS SECTION 👇👇👇👇👇👇 https://chat.whatsapp.com/BoRRwG9bqUFBt4djqzcNbb 𝗧𝗔𝗣 𝗧𝗛𝗜𝗦 𝗟𝗜𝗞𝗘 𝗧𝗢 𝗝𝗢𝗜𝗡 𝗠𝗬 𝗣𝗢𝗦𝗧𝗜𝗡𝗚 𝗥𝗢𝗢𝗠 👇👇👇👇👇👇👇 https://chat.whatsapp.com/LWmuu0yv6C9DAhpdepDb4i _________________✦✦✦✦✦✦✦✦✦✦✦✦✦✦✦__________________ PAGE ............14.........❤🥂 bakin gadon ya nufa ya zauna ya fara latsa wayar shi bai fi two minutes da zama ba , Ummi ta turo kofar dakin ta shigo ta na sallama ta na rike da tray din Fruits ta na ganin Hayat a kassa , ta zaro idanu ta na kiran sunan ta da karfi ta nufi table din gaban Sofa ta ajiye tray din hannun ta ta dawo wajen Hayat ta Zube saman guyiwowin ta ta talabo kan ta ta na kiran sunan ta amma shiru Hayat ba ta motsa ba " Ash me ya same ta " ta tambayi Ash ta na dago kai ta kaleshi sai da ya dan dauki lokaci kafin ya ce mata " i don't know , kawai tambayar ta na yi , sai na ga ta fadi " kare mishi kallo da kyau Ummi ta yi kafin ta ce mishi " Ash tell me the truth " ba tare da ya dago kai ba ya ce mata " karya zan miki ne , please ni fidda min ita da ga cikin daki " ba ta ce mishi komai ba ta tashi ta fito parlour nan ta tardo Junior ko motsi bai yi ba da ga wajen shi " please Marshal ko za ka iya dauko Hayat ka kai ta bedroom di na " ta fada mishi cikin sanyin murya " why ? me ya same ta ne ? " ya fada dan lumshe idanun ta ta yi a hankali kafin ta ce " please ka je ka dauko ta kawai " ba musu ya tashi ya nufi bedroom din Ash , ya na shiga ya ga Hayat konce kamar gawa bai tsaya bin ta kan Ash ba ya tsuguna ya sa hannu ya dauki Hayat cak kamar baby , ya juya ya fice bedroom din a haka ya fito part din dauke da Hayat Ummi na biye da bayan shi su ka sauko stair Nihal na ganin Junior dauke da Hayat ta mike ta na fadin " junior me ya same ta kuma ? " da sauri Ummi ta ce mata " kar ki damu mummy ina ga tsorata ta yi da ganin Ash " ta fada dan ta san abun da dan uwan ta ya aikata , sarai ta ga shatin hannun shi saman wuyan ta amma ta kyale shi sai da ta raka junior har bedroom din Hayat , ya kontar da ita saman bed din ta sannan su ka juyo a tare su ka baro part din su ka dawo parlour su ka zauna saman sofa guda su na zama Vedad ya ce ma Ummi " Big Sister , me ya same ta wai ? " dan karamin murmushi Ummi ta yi kafin ta ce " nothing my angel " da sauri Nihal ta katse ta da cewa " ki fadi gaskia dai , na san halin ki ba ki son abun da ya taba dan uwan ki " yar dariya Ummi ta yi kafin ta ce " Really mummy ba abun da ya same ta " " ni fa mummy ina ga Big bro ya fada soyayyar yarinyar nan " Iqbal ya fada cikin zolaya ya na yar karamar dariya dariya sosai junior ya yi kafin ya ce " wanene ? General da soyayya ? Kam ai duk wadda ta bude baki ta ce ta na son General sai ta mutu lokacin ta bai yi ba , wannan mai Taurin zuciyar bai san minene so ba " hararrar shi Ummi ta yi kafin ta ce " Junior kar fa ya jiyo ka " da sauri Junior ya kumshe dariyar shi , dan ya san indai Ash ya jiyo abun da ya ce yau sai ya kwana a word room " Mummy ni fa akwai wani abu da ban gane ba har yanzu ! " Iqbal ya fada ya na kallon Nihal daga mishi gera guda ta yi ta na fadin " minene abun kuma ? " " mummy why big bro ya ki duba Hayat jiya , ki na gani har da A box ya taho amma kuma ya ce ba zai iya duba ta ba bayan kuma har ya sauko , in da ba shi da niyar duba ta da ba zai sauko ba " gyara zaman shi Junior ya yi kafin ya ce " ka sani ko , wlh ni ma wannan abun ya tsaya min a rai , ban taba ganin Razana a cikin idanun General ba sai a lokacin " kallon shi Ummi ta yi kafin ta ce " Ban gane ba kenan sai da ya gan ta sannan ya ce ba zai duba ta ba ? " a tare junior da Iqbal su ka gyada mata kai allamun eh shiru ta yi ba ta ce komai ba , ita sai yanzu ta tuno a ranar dai'dai ta fito da ga cikin part din ta , ta ji zuciyar ta ta buga da karfi har sai da ta tsaya ta na karanto kalmar shahada ta rasa dalilin haka , kenan zuciyar Ash ce ta buga da karfi haka ta yi nisa cikin tunanin ta ta jiyo Muryar Iqbal ya na fadin " May be shi ma love at first sight ne ya ji " a tare shi da junior su ka bushe da dariya hannu Nihal ta kai ta buge Iqbal dama geffen ta ya ke juya wa ya yi ya kali Nihal ya ce " mummy why za ki bugu na , ni fa gaskiya ce na fada " " Mummy , Iqbal fa ya yi gaskiya , ita fa soyayya ba ka san lokacin da ta ke kama ka ba , ko ni haka na ji lokacin da na kamu da soyayya " Junior ya fada ya na yar karamar dariya yar karamar dariya Nihal ta yi kafin ta ce " Ku dai ku na son takurawa Ash , me ya yi muku ? " Ummi na shirin magana Vedad ya riga ta cewa " uhm uhm ni ku yi shiru don Allah kun hana ni kallon film di na " ya fada cike da shagwaba yar karamar dariya Iqbal ya yi kafin ya ce " Cutie Pie , Daddy once said ? " " Mummyn ku wayo ta ke min wlh " Vedad ya fada ya na dariya dariya Nihal ta yi kafin ta ce " Yanzu tsakani da Allah ni da Daddyn ku , wa ke yi wa wani wayo ? " " Gaskiya mummy ke ki ke yi mishi wayo " Ummi ta fada ta na yar dariya juyawa Iqbal ya yi kafin ya kali Ummi ya ce " Big sister , Daddy once said ? " dan jinkirtawa Ummi ta yi kafin ta ce " Alyasat ka rage wannan zuciyar ta ka " " ni dai ban taba jin Daddy ya ce haka ba " Iqbal ya fada yar karamar dariya Ummi ta yi kafin ta ce " ai ita mummy ba za ta manta ba " ta kai karshen ta na kashewa Nihal ido guda kafin ta bushe da dariya hararrar wassa Nihal ta yi mata kafin ta ce " za ki ga aiki na " kallon Junior Iqbal ya yi kafin ya ce " Marshal Daddy once said ? " matsowa bakin sofar Junior ya yi ya na kallon Iqbal ya ce " Ka na ji ko , kar ka dauko wannan rawan kai irin na mahaifin ka , wani lokacin ba shi da hankali " bushewa da dariya duk su ka yi sannan Vedad ya ce " Iqbal , Daddy once said ? " daga kan shi sama Iqbal ya yi kamar mai tunanin wani abu sannan ya sauko ya ce " baby na ne , kin manta i'm pregnant " dan karamin tsaki Nihal ta yi ta na murmushi ta kauda kai gefe ta ce " yau dai Daddyn ku ya shiga uku " da sauri Ummi ta ce " To mummy saura ke , Daddy once said ? " wani cool murmushi Nihal ta saki kafin ta ce " My beautiful wife " a tare duk su ka bushe da dariya da allamun madam ta tuno da mijin ta sai da su ka tsagaita dariyar shi sannan Iqbal ya ce " Ummi , mummy once said ? " " ke Ummi ba na hana ki yi mana irin wannan sabkon ba " Ummi ta fada ta na kallon Nihal kallon junior ya yi sannan ya ce " Marshal , mummy once said ? " dan satar kallon Nihal ya kafin ya ce " Abban Ummi " hararrar wassa Nihal ta mishi ta na fadin " yanzu junior har da kai " dariya sosai Junior ya yi har da kontawa saman Sofar sai da ya tsagaita ta dariyar shi sannan Iqbal ya kali Vedad ya ce " Cutie pie , mummy once said ? " cike da shagwaba ya ce " My angel " ya kai karshen ya na turo dan bakin nan nashi yar karamar dariya Nihal ta yi kafin ta kai hannu ta shafi kan shi ta ce " My angel " yar karamar dariya Vedad ya yi kafin ya ce ma Iqbal " Iqbal mummy once said ? " " Gaskiya baby ka hadu " ya kai karshen ya na satar kallon Nihal ta wutsiyar ido salati Nihal ta yi kafin ta ce " yanzu Iqbal yaushe ka ji na ce hakan ? " Ummi ta amsa mishi da cewa " Mummy duk fa abun da ku ke da Daddy mu na sane da shi , Iqbal ka na tune da wakar nan da Daddy ke yawwan yi wa mummy in ta na fushi da shi " da sauri Vedad ya ce " yeah i remenber , ko dazu sai da ya rera ta " tabe baki Nihal ta yi kafin ta ce " nan gaba sai na daina magana a gaban ku " yar karamar dariya Iqbal ya yi kafin ya ce " daga baya kenan " ya na gama fadar haka Vedad ya kali junior ya ce " Marshal , Big bro once said ? " dan zaro idanu su ka yi dukkan su har Ummi da Iqbal su na hada baki su na cewa " rufa mana asiri ba mu shirya yin jinya ba " bushewa da dariya Vedad da junior su ka yi , dama Vedad da gangan ya ce musu hakan ya san ba wanda zai iya ba da amsa sai da Junior ya tsagaita dariyar shi sannan ya ce " Big bro once said I hate love story " ya na gama fadar haka ya juya ya kali Nihal ya ce " mummy , His excellency once said ? " shiru ta yi na dan lokaci kafin ta ce " Tuzuru bai ji dadin rayuwar shi ba gaskiya " a tare duk su ka yi dariya , dan wannan maganar kullum sai Rayan ya fade ta duk lokacin da ya ga Nihal da Aylan tare kukan shagwaba Vedad ya fara yi musu ya na cewa " please Big bro once said ? " " ka san Allah Vedad ka ba mu lafya da Big bro , ba mu shirya jinya ba " Iqbal ya fada ya na hararrar shi " okay ku tsaya ni bara na fada muku " Nihal ta fada yar karamar dariya Vedad ya yi kafin ya ce " yawwa mummy , big bro once said ? " dan jinkirtawa Nihal ta yi kafin ta ce " Kai min su dakin horo " " kai , big bro ya na son wannan kalmar wlh " Iqbal ya fada junior ya karbe zancen da cewa " Allah kuwa , kamar a bakin shi a ka yi ta " " sai ma in ya ce If not " Vedad ya fada ya na bushewa da dariya har hada baki Ummi da Nihal su ka yi su na cewa " wlh in ya jiyo ku , ba ruwa na " da sauri Iqbal ya ce " no mummy , har da ku , ai tare mu ka yi hirar " girgiza mishi kai Nihal ta yi kafin ta ce " oun oun , ai ni ko ya ji ni ba abun da zai min ku ne dai zai cewa a kai ki dakin horo " matse gera junior ya yi kafin ya ce " mummy sai dai ya ce ma Vedad and Iqbal amma ban da ni " juyowa Ummi ta yi ta kale shi kafin ta ce " na lura yaron ga mugun son girma gare ka kamar dollar " dan karamin murmushin geffen fuska ya yi kafin ya ce " ba na girme ku ba ne ? wajen nan fa duk na girme ku har shi kan shi General " ya na gama fadar haka ya ga Vedad ya konta saman sofar ya hauda kan shi saman cinyar Nihal ya na kallon ta ya ce " mummy yi mana tatsuniya " dan zaro idanu Nihal ta yi kafin ta ce " My angel tatsuniya kuma ? ni dai ban da tatsuniyar da zan muku gaskia " ba ta gama rufe bakin ta ba , ta ga shi ma Iqbal ya konta ya tada kan shi da dayan cinyar ta ya na kallon face din ta ya ce " to ki ba mu labarin Daddy " yar karamar dariya ta yi ta na kai hannu saman kan yaran nata cike da so da kauna ta ce " wane irin labari kuma kun San komai game da Daddyn ku " " no mummy , something that you are the one who know This " Junior ya fada cikin sanyin murya dan jinkirtawa ta yi kafin ta ce " ounnnnnnn , Daddyn ku ba ya son a na mishi birthday party " " amma kowace shekara sai mun yi mishi , kuma bai taba cewa ba ya so " Iqbal ya fada ba tare da ya dago kan shi ba gyada musu kai ta yi kafin ta ce " yeah bai taba cewa ba ya so ba saboda farin cikin da ya ke ganin ku a ciki duk lokacin da ku ka shirya mishi Surprise birthday party , amma har cikin ran shi ba ya son ta , ko wannan Happy birthday da a ke ce mishi ba ya so , kawai ya na dannewa ne , dan kar ya bata muku " " but mummy , why ba ya son a na celebrated birthday din shi , amma kuma namu ko wace shekara shi da kan shi ya ke shirya mana ita " Junior ya fada ya na kallon Nihal dan karamin murmushi ta saki kafin ta ce " i don't know why , na sha tambayar shi amma bai taba bani amsa ba , why ba za ku tambayi General ba ? kun ga ai shi ma ba ya son birthday party may be dalilin su guda " dan karamin gunguni Iqbal ya yi kafin ya ce " mummy shi fa big bro duk wanda ya ce zai biye mishi sai ya mutu lokacin shi bai yi ba " yar karamar dariya Nihal ta yi kafin ta ce " why za ka cewa haka " " shi dai wani mutum ne gashi nan Allahu Alam , ba za ka taba gane inda ya dosa ba " cikin nitsuwa Junior ya katse shi da cewa " ni fa gaskiya ina tausayawa Matar da za yarda ta so wannan mai Taurin zuciyar , mutumin da ko murmushi gagarar shi ya ke " Kallon shi Ummi ta yi ta na cewa " kar ka tausaya mata , na san duk yarinyar da ta zama matar shi , za ta ji dadin rayuwar ta " da sauri Junior ya katse ta da cewa " Ummi ni fa na san dalilin da ya sa na ce miki , General sam ba zai iya kula da mace ba , ba ci da sha ba , wannan na san zai iya kula da su , amma kuma ta na da wasu hakki a kan shi wanda na san ba zai iya cika su ba " gyada kan Nihal ta yi kafin ta ce " wane irin Hakki kuma wanda ba zai iya cika wa ba ? " ta fada ta na yi mishi irin kallon nan na me ka ke nufi bayan kuma sarai ta gane abun da ya ke nufi yar karamar dariya ya yi kafin ya ce " mummy ina nufi , ba zai iya cika hakkin shi na aure ba , ko da ya yi aure ba na tunanin zai iya kusantar ta , shi fa sam ba ya sha'awar mace a rayuwar shi , ni fa na taba tardo wata Yarinya naked a cikin office din shi , amma ko dago kai bai yi ba bare ya kale ta " cikin nitsuwa Nihal ta katse shi da cewa " kar ka damu har ya samu matar komai zai cenja , Babu ta inda General ya baro mahaifin shi har sha'awar su kawai ya na dannewa ne " ba ta gama rufe bakin ta ba Vedad ya ce mata " mummy minene sha'awa kuma ? " murmushi mai dan sauti ta yi kafin ta na shirin magana ta jiyo a na musu gyaren murya da ga baya a tare duk su ka kai duban su a wajen stair din sai da su ka ji zuciyoyin su sun buga , ya na tsaye bakin stair ya na rike da hannayan shi a baya ya na kallon su kowane cikin ranshi ya na rokon Allah ya sa bai ji abun da su ke cewa ba gashi ko saman shi su ke magana bai ce musu komai ya sauko stair din ya karaso cikin parlourn ya nufi sofa three seaters ya zauna irin zaman nan na kasaita ya zuba mishi idanu babu ko kiftawa shiru kowa ya yi su na yi wa junan su kallon kallo amma ba wanda ya iya cewa ufan su na a haka Su ka Vedad ya mike zaune ya na kallon Ash ya ce " yawwa big bro kai ba bari na yi maka , Daddy once said ? " ya kai karshen ya na saki wani murmushi shiru Ash ya yi bai ce musu komai ba ya na dai bin su da kallo sai da ya share wajen good ten minutes a haka kafin ya bude baki a hankali ya ce " I have a wonderful Family " ya kai karshen ya na kallon Nihal wani cool murmushi ta saki kafin ta ce musu " shikenan ku tashi lokacin sallat ya yi " " okay mummy " Ummi ta fada ta na mikewa ta fara takawa ta shige corridor shi ma Junior ya mike ya Haye war shi Stair a tare Iqbal da Vedad su ka , amma kafin su tafi sai da su ka sunkuyo a tare su ka mannawa Nihal kiss saman kumatun ta sannan su ka Haye stair a tare parlour ya rage da ga Nihal sai Ash tsayawa ta yi ta na bin shi da kallo har ta dauki lokaci kafin ta bude baki a hankali ta ce " Gobe ina son na meda yarinyar nan gidan su " dan jinkirtawa ya yi kafin ya ce mata " wace yarinya ? " " wadda ka ki dubawa jiya " Nihal ta fada ta na sakin murmushi kauda kan shi gefe ya yi ya na cewa " I can't remenber " murmushi mai dan sauti ta yi kafin ta ce " shikenan , ka sa a shirya mana motocin da za mu tafiya Nijer din " slowly ya juyo da kan shi ya kale ta ya ce " Nijer kuma ? " gyada mishi kai ta yi a hankali kafin ta ce " eh , Da ga Nijer ta ke , Kauyen NAWACH KALE " " okay zan sa Felix ya kai ku , karfe nawa za ku tafi ne ? " " bayan Sallar asuba , ba na son mu kai dare ba mu isa ba cikin kauyen ba " gyada mata kai kawai ya yi kafin ya mike ya fara takawa a hankali ya nufi stair ya Haye da kallo ta raka shi har sai da ya Haye sannan ta saki wani cool murmushi ta ce " i really love you My Beautiful wife " ta na gama fadar haka ta tashi ta nufi corridor ta shiga part din ta ▪ASH 🔥 kai tsaye bedroom din shi ya wuce , ya na shiga idanun shi su ka sauka saman tray din fruits din Ummi ta kawo mishi a hankali ya nufi Sofar ya zauna ya janyo table din gaban shi ya kai hannu ya fara sha cikin konciyar hankali ko one minute bai yi ba da zama Vedad ya turo kofar ya Shigo , Iqbal na biye da bayan shi ya na sallama kassa kassa kai tsaye Bed din shi Iqbal ya nufa ya zauna Vedad kuma ya nufi Sofa ya zauna geffen Ash ya kai hannu ya fara daukar fruits shi ma ya na sha a hankali ya dago kai ya kali Ash ya ce " Big bro what means Sha'awa ? " ba tare da ya kale shi ba ya ce " I don't know " turo dan bakin nan nashi Vedad ya yi kafin ya ce " ka sani , kawai ba ka da niyar fada min " " Get out " Ash ya fada cikin sanyi murya nan take Vedad ya shiga yi mishi kukan shagwaba har da bubuga kafafun shi a kassa kafin ya mike ya fice dakin da kallo Iqbal ya raka shi har sai da ya fita sannan ya bushe da dariya har da kontawa saman gadon ya na tsaka da dariyar shi ya jiyo Muryar Ash ya na fadin " Where is your girlfriend " tsagaita dariyar shi Iqbal ya yi kafin ya mike zaune ya kali Ash ya ce " which girlfriend ? " ba shiri Ash ya dago kan shi ya kali Iqbal ya ce mishi " your girlfriend Maya ? " " ohhhhhh Maya , ta na nan lafya , jiya ma mun yi waya da ita " " me ta ce maka ? " dan jinkirtawa Iqbal ya yi kafin ya ce " ta ce min na yi sauri na dawa idan ba haka ba mantawa zan yi da ita " " ka na iya mantawa da ita kenan " yar karamar dariya Iqbal ya yi kafin ya ce " I think Yeah ! ni na ma manta ina mu ka hadu wlh " cikin nitsuwa Ash ya katse shi da cewa " ba university din ku guda ba ? " girgiza mishi kai Iqbal ya yi kafin ya ce " no , gaskiya na manta a ina mu ka hadu , may be a cikin university din ne , ko kuma wani wajen daban , who know ? " MY BOOK IS ONLY ₦300 VIA 8081129487 Khadija Sabi'u Monie point bank KU TURA SHAIDAR BIYAN TA WANNAN NUMBER +22795577612 or +22798999753 TAღRIN ZღCIYA 💖🌺💍 ( RETღRN ) (ROMANTIC LUV STORY )💋🔥 ❤👑 ꪑꪖꪶꪶꪖƙỉ᭢ ᩏꪹỉ᭢ᨶꫀకక ꪑꫀꫀꪹꪖꫝ 👑❤ 🕊💞 Wattpad : @bennybite Marubuciyar littafin TAURIN ZUCIYA EXILED PRINCE ( LOVE MEETS POWER ) TWO LIGHTS ( YAR JARIDA ) and now TAURIN ZUCIYA ( RETURN ) FOR MORE INFORMATION KU TABO WANNAN NUMBER +22798999753 WHATSAPP ONLY , Thanks 👍💕 اللَّهُمَّ صَلِّ عَلَى مُحَمَّدٍ وَعَلَى آلِ مُحَمَّدٍ، كَمَا صَلَّيْتَ عَلَى إِبْرَاهِيمَ وَعَلَى آلِ إِبْرَاهِيمَ، إِنَّكَ حَمِيدٌ مَجِيدٌ، اللَّهُمَّ بَارِكْ عَلَى مُحَمَّدٍ وَعَلَى آلِ مُحَمَّدٍ، كَمَا بَارَكْتَ عَلَى إِبْرَاهِيمَ وَعَلَى آلِ إِبْرَاهِيمَ، إِنَّكَ حَمِيدٌ مَجِيدٌ️ TAP THIS LINK TO JOIN MY WHATSAPP GROUP COMMETS SECTION 👇👇👇👇👇👇 https://chat.whatsapp.com/BoRRwG9bqUFBt4djqzcNbb DOMIN SAMUN BOOK DI NA DA GA FARKO ZA KU IYA ADDING CHANEL DI NA TA WANNAN LINK 👇👇👇👇👇👇 https://whatsapp.com/channel/0029VaGhJCqKmCPUvpvIJ80i 𝗧𝗔𝗣 𝗧𝗛𝗜𝗦 𝗟𝗜𝗞𝗘 𝗧𝗢 𝗝𝗢𝗜𝗡 𝗠𝗬 𝗣𝗢𝗦𝗧𝗜𝗡𝗚 𝗥𝗢𝗢𝗠 👇👇👇👇👇👇👇 https://chat.whatsapp.com/LWmuu0yv6C9DAhpdepDb4i _________________✦✦✦✦✦✦✦✦✦✦✦✦✦✦✦__________________ PAGE ............15.........❤🥂 shi dai Ash da ido kawai ya ke bin shi , kafin su taho Nigeria Iqbal ya fada mishi wani abu daban a kan ta , shi kuma abun da ya gano daban , yanzu kuma abun da Iqbal ke fada mishi daban , tabass akwai wata a kassa , shi ya san akwai wani boyayen al'amari a cikin familyn shi wanda ba a fada mishi ba , amma Maya ita kuma da ga ina , ta ya za ka mance mutumin da ka ke so haka lokaci guda har ka manta a ina ku ka hadu tabass akwai wani abu a kassa ya yi nisa cikin duniyar tunanin shi ya jiyo Muryar Iqbal ya na fadin " Big bro tunanin mi ka ke haka ? " slowly ya dawo cikin hayacin shi kafin ya ce mishi " zan iya ganin Pics din ta ? " gyada mishi kai Iqbal ya yi kafin ya kai hannu cikin Aljihun trouser din shi ya fido wayar shi ya fara latsawa sannan ya mikawa Ash wayar ya na fadin " ga ta nan " hannu ash ya kai ya karbi wayar ya na kallon Screen din slowly ya dago kai ya kali Iqbal kafin ya Meda kallon shi kan wayar , sannan ya mikawa Iqbal kayan shi hannu ya kai ya karba sannan ya mike ya fice dakin da kallo Ash ya bi shi har sai da ya fita sannan ya kai hannu cikin aljihun shi ya fido wayar shi ya fara latsawa sai da ya dauki wajen good five minutes kafin ya kai wayar a kunne murya cen kassan makoshi ya yi sallama sannan ya ce " in sha Allah next week ina dawowa US , akwai wani abu da na ke son mu tatauna a kai " ya na gama fadar haka ya sauko wayar ya katse kiran ya ajiye wayar saman table sannan ya mike ya nufi toilet ya shiga ▪MISALIN KARFE 12 NA DARE ▪HAYAT 💦 A hankali ta fara motsi ta na kokarin tashi ta na bude idanun ta ta fara tari , ta na kai hannu ta na shafa wuyan ta slowly ta mike zaune ta na karanto kalmar shahada , ta na bin dakin da kallo kamar bakon ta sai da ta dauki good ten minutes a haka kafin ta sauko da kafafun kassa ta mike tsaye ta nufi kofar fita dakin ta fito parlour kai tsaye part din ta fito ta na tafiya a hankali kamar wanda a ka zarewa lakar jiki a haka har ta fito parlourn gidan , amma sai ta ga ba kowa tsaya wa ta yi ta na bin wajen da kallo ta na cewa " Aunty Ummi ? " ta fada ta na karasowa cikin parlourn tsaya wa ta yi ta na bin wajen da kallo amma ba kowa ita sam ba ta san da dare ya yi ba saboda Hasken wajen Slowly ta juyo za ta bar wajen kawai sai ji ta yi ta bugi kirjin mutun da sauri ta yi baya ta na cewa " yi hakuri " ta kai karshen ta na dago kai ta kale shi dum ta ji zuciyar ta ta buga da ci karo da wadanan Sexy blue eyes din na shi nan take duk abun da ya faru ya dawo mata a kai har ta bude baki za ta saki kara ya yi sauri ya kai hannu ya toshe mata baki ya na kallon cikin idanun ta ya ce " idan ki ka kuskura ki ka yi min kara sai na kashe ki a wajen nan " wasu wahalalun yawu ta hadiye dan ba karamin razana ta yi ba specially da ta tuno irin shakar da ya yi mata dazu da safe nan take tsoron shi ya shige ta slowly ya zame hannun shi ya ce " wacece ke , su wa su ka aiko ki , me ya sa ki ka kashe matar nan ? " a hankali ta fara girgiza mishi kai ta na cewa " ni ban san abun da ka ke cewa ba " ta fada dan da turanci ya ke mata magana a dubu dari ya kai hannu ya damko wuyan ta ya ware idanun shi da kyau ya na kallon cikin nata ya ce " kar ki ce za ki raina min hankali , su wa su ka aiko ki na ce " nan take idanun ta su ka kawo ruwa hawaye na zubo mata ta lumshe idanun ta dan ba za ta iya jure kallon cikin nashi ba rage shakar da ya yi mata ya yi kafin ya ce " open your eyes " slowly ta fara bude idanun ta , sai cikin nashi ko Dum ya ji zuciyar shi ta buga , ba shiri ya saki wuyan ta ya ja da baya slowly ya juya ya ba ta baya ya lumshe idanun shi cikin zuciyar shi ya na cewa " Alyasat ka kontar da hankalin ka , it's just a dream , dream it's not true , it can't be true Never " ajiyar zuciya ya sauke kafin ya bude idanun shi ba tare da ya juyo ba ya ce mata " Wacece ke , minene sunan ki ? " murya na kerma ta ce mishi " suna na Shahd " ta kai karshen kamar za ta yi kuka dan zaro idanu ya yi ya na maimaita sunan cikin zuciyar shi cen kuma sai ya ce mata " matar da ki ka kashe wacece ita , minene hadin ki da ita ? " a hankali ta saki kuka ta na cewa " ni ban kashe ta ba , sayar da ni ta so yi shi ne na gudu , don Allah kar ku kaini wajen yan sanda " bai ce mata komai ba ya nufi stair ya haye ya koma part din shi ta na ganin ya haye stair ta nufi corridor da gudu ta shige part din Ummi , ta koma bedroom din ta ta Haye gadon ta dunkule waje guda ta na kuka ta na fadin " ni wajen Inna ta zan koma , don Allah ku meda ni wajen inna ta " ta kai karshen ta na kara sautin kukan ta a haka har barci ya dauke ta ▪ASH 🔥 kai tsaye part din shi ya koma ya na shiga bedroom din shi ya ga Vedad konce saman bed din shi ya yi daya daya ya na barci bai ce mishi komai ba ya nufi toilet ya shiga ya yi wanka jim kadan ya fito sanye da bathrobe ya shiga dressing room ya shirya cikin kayan barcin shi farare kal , ya nufi bed din shi ya Haye geffen Vedad ya konta ya kai hannu ya kashe lamps din dakin ya kunna bedside lamps ya kara gudun ac sannan ya lumshe idanun shi ya na lumshe su ya jiyo Muryar Vedad ya na fadin " Big bro , ka ce mata ta baro min bedroom di na " ya kai karshen cikin shagwaba slowly Ash ya juyo ya kale shi ya ce " My angel , kai da wa kuma ? " a hankali Vedad ya bude idanun shi ya turo dan bakin nan nashi ya ce " ba da kai na ke ba , ni ka je ka ce mata ta baro min bedroom " cikin rudu Ash ya ce mishi " wacece cikin bedroom din ka ? " " Big bro ni ma ban san ta , kawai da na rufe ido na , sai ta yi ta tabo ni , ni ka je ka ce mata ta baro min bedroom ko kuma na kwana a nan " " me ya sa kai ba ka taba ta , tashi ka je ka ce mata ta kyale ka , ko kuma ka kashe ta " ya na gama fadar haka ya juya ya na fuskantar ceiling ya lumshe idanun shi kukan shagwaba Vedad ya fara yi mishi ya na fadin " big bro , ba ta jin magana ta , sai da na ce mata ta kyale ni amma ta ki dainawa , ita wai sai ta ga abun da ke cikin trouser di na " ya na gama rufe bakin shi ya jiyo Muryar Iqbal ya Bushe da dariya ashe tun lokacin da Vedad ya fara magana ya ke tsaye bakin kofar dakin ya na sauraron shi sai da ya Kamala dariyar shi sannan ya shigo dakin ya na sanye da kayan barcin shi , shi ma farare kal kamar na Ash ya nufi bed din ya Haye ya na kallon Vedad ya ce " Cutie pie , irin wannan mafarkin ka fara yi kennan ? " hararrar shi Vedad ya yi ya na fadin " ni ba mafarki na yi ba , kuma mu je ka gan ta cikin bedroom di na , ka ce mata ta bar min bedroom " dariya sosai Iqbal ya yi har da kontawa ya na dafe ciki kukan shagwaba Vedad ya shiga yi mishi ya na fadin " ni ka daina min dariya ko na fadawa mummy " tsagaita dariyar shi Iqbal ya yi kafin ya matso da kan shi ya kai bakin shi saitin kunnen Vedad ya rada mishi " ka na ji ko Next time idan ta dawo ka kyale ta , ta duba abun da ke cikin trouser din ka , da ga nan ba za ta sake dawowa ba " noke mishi kafada Vedad ya yi ya na cewa " no ni ba zan kyale ta ba , sai dai mu je ka ce mata ta kyale ni , ko kuma na sa gun na harbe ta " " ba sai an kai ga haka ba , kai dai ka kyale ta ta duba za ta ga abun da ya fi karfin ta " " da gaske ? " Vedad ya fada ya kallon Iqbal ta wutsiyar ido gyada mishi kai Iqbal ya yi ya na sakin wani makirin murmushi a hankali Vedad ya mike zaune , Ya kai hannu a hankali ya riko wandon barcin Ash ya yi sama da shi ya leka dan karamin tsaki Vedad ya saki kafin ya saki trouser din Ash ya juyo ya kali Iqbal da ke faman Zaro idanu ya ce " yo ai ni ban ga abun da ya fi karfi na ba " ya fada dan ya ga Ash ya na sanye da Short kassan wandon shi Iqbal bai ce mishi komai ba ya sauko da kafafun shi kassa , ya fara takawa a hankali kamar barawo ya nufi hanyar fita bedroom din sarai Ash ke lure da shi , sai da ya bari ya kai bakin kofar dakin sannan ya diro da kafafun shi kassa a dubu dari ya damko shi ta baya ya daga sama ya tila shi saman bed geffen Vedad wata yar karamar kara ya saki kamar zai yi kuka ya ce " wayooo mummy ya karaya min baya " da sauri Ash ya ce mishi " yi min shiru ko kuma na harbe ka " ya na gama fadar haka ya koma inda ya taso ya konta ya lumshe idanun shi ya aza hannun shi guda saman forehead din shi dariya sosai Vedad ya ke ya na kallon Iqbal da ke faman murkuso saman bed din ya marairaice fuska kamar zai yi kuka ya na tsaka da dariyar shi Ash ya kai hannu ya damko bayan wuyan shi ya na fadin " kai kuma me ka ajiye cikin trouser di na ? " shagwabe fuska ya yi ya ce " Iqbal ne ya ce min na duba zan ga abun da ya fi karfi na " da sauri Iqbal ya ce " Wlh big bro ban ce ba ya duba , Vedad sharri za ka min " Vedad na shirin magana Ash ya ce musu " ku yi min shiru , zan yi maganin ku , ku tabbatar na tarda ku a dakin horo gobe " ya na gama fadar haka ya janye hannun shi da ga bayan wuyan Vedad ya Meda saman cikin shi ya lumshe idanun shi dan karamin gunguni Iqbal ya shiga yi murya kassa kassa ya ce ma Vedad " bari mu koma part din mu za ka ga aiki na " murguna mishi baki Vedad ya yi kafin ya juya ya rungume Ash kamar ya samu wani Teddy ya lumshe idanun shi , ba jimawa barci ya yi gaba da shi haka zalika Iqbal Ash kuma dama ba barci ya ke ba , kawai dai ya lumshe idanun shi ko cen dama ba wani barci ya ke ba , dalilin da ya sa ma ya ke yi wa kan shi Allurar barci dan sai ya yi kwana uku idon shi biyu kuma babu gajiya dan kamar robot ya ke tun lokacin da Aylan ke a raye da ya fara ba shi training din Soja ya koya mishi wannan rashin kwanan , dan sai ya saka shi cikin daki ya ce sai ya yi kwana biyu a ciki kuma kar ya sake ya rufe idanun shi da sunnan zai yi kwana da haka har ya saba bayan ya shiga millitary camp kuma nauyin barcin shi ya bace , dan ko nunfashi sama sama ka yi geffen shi in ya na barci sai ya farka , wani lokaci idanu bude ya ke barci duk cikin training din da ya samu ne , Ash fa soja ne mai zaman kan shi dan karyar mutum ya ce zai gwada mishi training din soja duk girman kato in Ash ya buge shi sai ya kai ga kassa a headquater din su da ya shigo waje kowa ke shan jinin jikin shi , ko wata magana za a yi mishi sai dai a fadawa Junior sannan ya je ya fada mishi , sam ba ya sakin musu fuska , kullum ta na a tsuke ya saka bakaken glass , dan wadanan sexy blue eyes din nashi kadai sun isa tsoratar da mutum , tun bayan rasuwar Aylan ya daina sakin fuska , ko murmushi yanzu tsawan shekara 15 har yanzu bai sake yin shi ba har ya ma manta yadda a ke yin shi dama dama in ya na gida ya na sakin musu fuska ya yi wassa da Vedad amma kuma in ya bata mishi sai Nihal da Rayan sun kwace shi dan dakin horo ya ke tafiya da shi sai ya kwana a ciki babu ruwa babu abinci ga shi kuma ba ya daukar raini , ko Rayan da kan shi ya yi wa Ash maganar rainin hankali sai Nihal ta shiga tsakanin su dan ba ya kyale shi , da ya tashi dauko Zuciyar Aylan sai da ya wuce shi ga kuma training din kwararen soja da ya samu zuciyar shi duk ta bushe ba dan ya na ganin girman Nihal a matsayin ta na mahaifiyar shi ba na san da ko ita ba zai kyale ta ba ▪MISALIN KARFE 5 NA SAFE misalin karfe biyar na safe bayan sun Kamala sallar asubahi , Nihal ta shirya za ta mayar da Hayat kauyen su tare da Vedad da Iqbal , tafiyar ta su ta wayo ce dan su tserewa Ash , Ummi kuma ta ce ita ba za ta je ba za ta jira su a gida cikin mota guda Nihal da Hayat su ka shiga , Vedad da Iqbal kuma su ka shiga mota guda , sai motocin guards din su a haka su ka baro gidan su ka kama hanyar Niger Hayat baki ya ki rufuwa yau za ta koma gida kamar ta yi furkakai ta ga kan ta cikin gidan su Nihal kuwa ba da Niyyar baro Hayat za ta je , tabass da ita za ta dawo ▪NIGER ( KAUYEN NAWACH KALE ) ▪ MISALIN KARFE 2 NA YAMMA zaune Barira ta ke cikin harabar gidan su , ta yi zugum waje guda duk ta rame har wani duhu ta yi , yanzu wajen sati guda kenan ba Hayat ba me kama da ita , har mutanan kauyen sun daina cigiyar ta ta na a haka Inna ta fito da ga cikin Dakin ta , ta karaso wajen tabarmar da Barira ke zaune ta zauna ita ma cikin sanyin murya ta ce " Barira , wai har yanzu ba za ki daina damuwar kan ki ba " wani dogon nunfashi Barira ta ja kafin ta ce " Inna ya ki ke so na yi , kin fi kowa sanin Hayat ita kadai na mallaka , ba zan iya rayuwa babu ita ba , ni yanzu babban abun da ke damu na shi ne halin da ta ke ciki , ta na cikin koshin lafya , ta na hannun mutane na gari ko kuwa , inna don Allah ku kawo min Hayat di ta " ta kai karshen ta na fashewa da kuka ba karamar karayawa Inna zuciya ta yi ba da kukan nan nata , tun da ta auri malam ba ta taba samun haihuwa ba , car Allah ya yi wa kanwar shi rasuwa su ka kamo Barira ta dawo wajen su da zama tun ta na da shekara bakwai , har ta yi aure ta haifi Hayat dole ta ji ba dadi saboda ita kadai ce yarinyar ta , ita kadai ce jika a cikin gidan idan wani abu ya same ta tabass ba za su ji dadi ba cikin sanyin murya Inna ta ce ma Barira " Don Allah ki kontar da hankalin in sha Allah ba abun da zai same ta " da sauri Barira ta katse ta da cewa " to inna ina ta ke , in har ba abun da ya same ta me ya sa ba ta dawo gida ba , Inna in ba za su iya tafiya neman ta ba , ku bar ni na je neman ta da kai na , don Allah Inna " hannu inna ta ja ta rungume Barira ta ce " Ki yi hakuri Barira ta , haba Diyar malam , jikar barbushi guda ko aljanu sun kyale ta bare mutum " inna ta fada cikin zolaya yar karamar dariya Barira ta yi kafin ta ce " Inna , wace jikar barbushi kuma , ku kyale min Hayat di ta da wasu aljanai , ni da ma zan iya yi musu magana da zan ce su je su kawo min Hayat di ta " yar karamar dariya inna ta yi ta na kai hannu ta buge ta kadan a baya ta na fadin " sannu mara kunya , ni za ki fadawa Haka ? sai na yi maganin ki " " Uhm uhm ni ki kyale ni mun ma bata , da ga ina yi miki wassa " hannu inna ta kai ta ja mata kumatu ta na fadin " na ji shikenan , ya kamata ki je ki yi sallat ki yi wa Hayat adu'a , a duk inda ta ke Allah ya kare miki ita , ya dawo miki da ita cikin koshin lafya " wani cool murmushi Barira ta saki ta ce " In sha Allah za ta dawo min lafiya , na san Hayat di ta jaruma ce , za ta iya kula da kan ta a duk inda ta ke , duk wani mugun abu da ya tunkaro ta Allah ba zai bari ya cutar da ita ba , Zan ci gaba da yin adu'a Allah ya tsareta a duk inda ta ke , ya medo min ita lafiya " da Ameen Inna ta amsa ma ta MY BOOK IS ONLY ₦300 VIA 8081129487 Khadija Sabi'u Monie point bank KU TURA SHAIDAR BIYAN TA WANNAN NUMBER +22795577612 or +22798999753 TAღRIN ZღCIYA 💖🌺💍 ( RETღRN ) (ROMANTIC LUV STORY )💋🔥 ❤👑 ꪑꪖꪶꪶꪖƙỉ᭢ ᩏꪹỉ᭢ᨶꫀకక ꪑꫀꫀꪹꪖꫝ 👑❤ 🕊💞 Wattpad : @bennybite Marubuciyar littafin TAURIN ZUCIYA EXILED PRINCE ( LOVE MEETS POWER ) TWO LIGHTS ( YAR JARIDA ) and now TAURIN ZUCIYA ( RETURN ) FOR MORE INFORMATION KU TABO WANNAN NUMBER +22798999753 WHATSAPP ONLY , Thanks 👍💕 اللَّهُمَّ صَلِّ عَلَى مُحَمَّدٍ وَعَلَى آلِ مُحَمَّدٍ، كَمَا صَلَّيْتَ عَلَى إِبْرَاهِيمَ وَعَلَى آلِ إِبْرَاهِيمَ، إِنَّكَ حَمِيدٌ مَجِيدٌ، اللَّهُمَّ بَارِكْ عَلَى مُحَمَّدٍ وَعَلَى آلِ مُحَمَّدٍ، كَمَا بَارَكْتَ عَلَى إِبْرَاهِيمَ وَعَلَى آلِ إِبْرَاهِيمَ، إِنَّكَ حَمِيدٌ مَجِيدٌ️ DOMIN SAMUN BOOK DI NA DA GA FARKO ZA KU IYA ADDING CHANEL DI NA TA WANNAN LINK 👇👇👇👇👇👇 https://whatsapp.com/channel/0029VaGhJCqKmCPUvpvIJ80i TAP THIS LINK TO JOIN MY WHATSAPP GROUP COMMETS SECTION 👇👇👇👇👇👇 https://chat.whatsapp.com/BoRRwG9bqUFBt4djqzcNbb 𝗧𝗔𝗣 𝗧𝗛𝗜𝗦 𝗟𝗜𝗞𝗘 𝗧𝗢 𝗝𝗢𝗜𝗡 𝗠𝗬 𝗣𝗢𝗦𝗧𝗜𝗡𝗚 𝗥𝗢𝗢𝗠 👇👇👇👇👇👇👇 https://chat.whatsapp.com/LWmuu0yv6C9DAhpdepDb4i _________________✦✦✦✦✦✦✦✦✦✦✦✦✦✦✦__________________ PAGE ______16_____ 🔥💦 Inna na gama rufe bakin ta wani yaro ya shigo da gudu cikin gidan babu ko sallama ya nufi gaban su Inna ya na faman haki ya ce " Inna Barira , ga wasu jibga jibgan sojoji tsaye bakin kofar gidan ki " kallon juna Barira da Inna su ka yi kafin Barira ta juyo ta kali yaron ta ce " Sojoji kuma baba Idi ? a kofar gida na , cewa su ka yi su na nema na ? " girgiza mata kai yaron nan ya yi kafin ya ce " Inna Barira ban sani ba , ni ma mu na wassa ne na gan su shi ya sa na taho na fada miki , kuma kuma na ga wata yarinya mai kama da Hayat a tare da su " dum Barira ta ji gaban ta ya fadi da sauri ta mike tsaye ta na zaro idanu ta ce " Baba Idi Hayat di ta ka gani tare da su ? " " Inna Barira , na ce miki mai kama da ita yarinyar nan fa yar burni ce idan ki ka gan sam ba ta yi kama da Hayat ba , idanun su ne kawai su ka yi kama " da sauri Barira ta nufi kofar fita gidan ta na rokon Allah ya sa Hayat din ta ce ta na kawo tsakiyar harabar gidan ta tsaya cak ta na kallon Hayat da ta nufo ta da gudu ta na hawaye da sauri Barira ta nufe ta ta rungume ta , ta na sakin kuka kamar karamar yarinya ta na fadin " Hayat ! Da gaske ke ce ? Allah na gode maka , Allah na gode maka da ka dawo min da Shahd di ta cikin koshin lafya " cikin kuka Hayat ta fadin " ni ce Inna , na yi kewar ki sosai Inna " Barira na shirin magana Nihal ta shigo gidan ta na sallama , Vedad da Iqbal na biye da ta da sauri Hayat ta raba jikin ta da Barira ta koma wajen Nihal ta riko hannun ta ta na fadin " Inna kin ga mummy , ita ce ta dawo da ni gida , mummy wannan ita ce Inna ta " ta kai karshen ta na nuna wa Nihal Barira a hankali Barira ta karaso gaban Nihal ta rike hannayan ta dukka biyu kamar za ta yi kuka ta ce " na gode da ku ka medo min ita , Ita kadai na mallaka a duniya " cikin nitsuwa Nihal ta katse ta da cewa " Shikenan ya isa haka , kar ki saka ni kuka ni ma " ta na gama rufe bakin ta Vedad ya karaso geffen Nihal ya marairaice murya ya ce " mummy please mu tafi , ba na jin dadin tsayuwa a wajen nan " cikin harshen Turanci Nihal ta ce mishi " My angel please calm down , ba za mu jima ba za mu koma " ta na gama rufe bakin ta su ka jiyo Muryar Inna ta na fadin " Barira sai ki bar su a tsaye ? ku karaso mana " da sauri Barira ta ce " don Allah mu je ku zauna , ko da ruwa ne ku sha na san kun debo hanya " ta kai karshen ta na nuna musu tabbarmar da Inna ke zaune ba musu Nihal ta tako a hankali ta na rike da hannun Hayat su ka karaso wajen Tabarmar su ka zauna dan karamin tsaki Vedad ya yi kafin ya juya ya fice , da sauri Iqbal shi ma ya juya ya bi bayan shi su ka koma cikin motar su su na barin wajen Barira ta juya ta nufi tulunan gidan ta debowa Nihal ruwa cikin girmamawa ta mika mata wani cool murmushi Nihal ta saki kafin ta kai hannu ta karbi cup din ruwan ta kai bakin ta , ta kurbi kadan sannan ta ajiye shi ta na yi wa Barira godiya zama Barira ta yi ta kai hannu ta janyo Hayat ta na bin ta da kallo ta ce " Hayat ina ki ka samo irin wadanan kayan , dubi yadda ki ka sauya lokaci guda haka , ba dai Shafe shafe ki ka yi a cen ba " yar karamar dariya Hayat ta yi kafin ta ce " Inna ba wani shafe shafe da na yi , kuma Aunty Ummi ta ba ni kayan nan , sun yi min kyau ? " wani kyawatencen murmushi Barira ta saki kafin ta ce " Sosai ma kuwa ni da farko kassa gane ki na yi , sai ka ce irin Gimbiyoyin nan da mu ke gani a cikin Tv kin gane su ai ? " dariya sosai Hayat ta yi har ga Allah ta yi kewar Innar ta , kuma ta godewa Allah da ya sa su Nihal ba kamar Hajiya ta ke ba , ga shi ta cika Alkawari ta medo ta wajen innar ta " oun don Allah ina son na yi magana da mahaifiyar ta " Nihal ta fada cikin sanyi murya gyada mata kai Barira ta yi kafin ta ce " Ina sauraron ki , wace magana kuma ? " wani cool murmushi Nihal ta saki kafin ta juya ta kali Hayat ta ce " don Allah ina son wata Alfarma a wajen ki " kallon Hayat ita ma ta yi cikin rudu ta ce " wace irin Alfarma kuma ? " dan sunkuyar da kai Nihal ta yi kafin ta dago ta kali Barira ta ce " na san ba za ki fahimce ni ba , amma ina jin Hayat sosai a ciki zuciya ta , ba na jin zan iya rabuwa da ita gaskiya , don Allah don son annabi Muhammad ( S.A.W ) ki bari na koma da Hayat , da na yi niyya ba abun da zai hana ni wucewa da ita america kai tsaye , amma kin ga sai da na medo miki ita saboda ni ma uwa ce , na san irin zafin da ki ka ji cikin zuciyar ki lokacin da ba ta nan , shi ya sa na medo miki ita dan ki san ta na cikin koshin lafya kuma ta fado a hannun mutanan kwarai , don Allah ki bari na koma da ita wlh ban jin zan iya rabuwa da ita " dan zaro idanu Hayat ta yi ta na kallon Nihal ai ko abun da zai raba ta da innar ta a yanzu sai dai mutuwa , ta dawo kenan babu inda za ta je bare kuma ta ga Ash a cikin gidan ta san wannan babu tsoro a cikin idanun shi tabas zai iya kashe ta watarana nan take ta fashe da kuka ta kankame Barira ta na fadin " Ni wlh babu inda zan je , ba zan bi ki ba , ni wajen Inna ta zan zauna " rungume ta da kyau Barira ta yi idanun ta na kawo ruwa ta ce " Haba baiwar Allah , ya za ki min haka , ni ina godewa Allah Hayat di ta , ta dawo , ke kuma ki na neman ki raba ni da ita har abada ? idan ta tafi America ina zan samu damar ganin ta , ita kadai ce Allah ya ba ni ya zan rabu da ita " cikin sigar rarrashi Nihal ta ce " za ta dinga dawowa , don Allah ki yi min wannan Alfarma ba dan na girme ki ba ? " da sauri Barira ta girgiza mata kai ta ce " a'a ba zan iya rabuwa da Hayat di ta ba gaskiya ki yi hakuri malama " har Nihal ta bude baki za ta yi magana wata zuciyar ta ce mata " ke tsaya , me zai hana ki tafi da su baki daya , kin ga Barira ba mumuna ba ce , da ta sha wanka za ta fito fess abun ta , ni da na ke da dan uwa zaune ba mata , lokacin kawo karshen gwaurancin yaya Rayan ne ya zo ba ki sani ba " wani kyawatencen murmushi Nihal ta saki kafin ta ce " me zai hana mu tafi tare har da ke ? " cak Barira ta tsaya ta na zaro idanu ta kali Nihal ta na shirin magana Nihal ta riga ta cewa " don Allah , tun da kun ce ba za ki iya rabuwa da ita ba , me zai hana mu tafi tare da ku baki daya " slowly Barira ta juya ta kali Inna , dan karamin murmushi inna ta saki kafin ta dafa shoulder din Barira ta ce " Barira ki yarda ku tafi tare da yarinyar ki , tun da har ta amince za ta tafi da ku ki yarda kawai " Inna ta fada don har ga Allah za ta so Barira ta tafi , ga shi cikin kauyen ba ta da koya sai ita da malam , su kuma shekaru sun ja ba za su iya kula da ita ga kuma Hayat , ga shi ba wasu gonaki gare su da za su ci albarkacin ta , Idan har Barira ta tafi da Nihal hankalin su zai fi konciya da sanin ko bayan rayuwar su akwai wanda zai kula musu da ita , da su bar ta cikin wannan duniyar babu dangin uwa bare na uba gwara su bar ta a hannu mutunan kirki da su ka yarda da kan su za su karbe ta cikin ahalin su Sunkuyar da kan ta Barira ta yi , kamar mai tunanin wani abu cen kuma ta dago kai ta ce " amma Inna ki na ganin malam zai yarda " " na san zai yarda , amma ku je na san ya na a fada yanzu sai ki tambaye shi " inna na gama rufe bakin ta Nihal ta dora da cewa " eh , eh zai yarda ma , don Allah kar ki ce a'a ki tashi mu je mu tambaye shi idan ya amince sai mu wuce " dan jinkirtawa Inna ta yi kafin ta raba jikin ta da Hayat ta ce " shikenan bari na hada kaya na " ta kai karshen ta na kokarin mikewa dan ta je ta gado kayan ta da sauri Nihal ta taro ta ta na cewa " kar ki damu , za mu saya miki kaya a cen idan mun je , kawai ki tashi mu tafi , ba na son mu kai dare ba isa cikin gari ba " kallon Inna Barira ta yi kamar za ta yi kuka ta rasa yadda za ta yi , ba za ta iya rabuwa Da Hayat ba , kuma ta na jin zafin rabuwa da inna matar nan ita ta kula da ita tun ta na yar shekara bakwai , har ta kai munzalin mutane su ka ba ta tarbiya me kyau , su ka shayar da ita , su ka tufatar da ita , su ka kai ta islamya , ta koyo sunnonin Sallat , karatun kur'ani su ka yi mata aure cikin amincin Allah ta samu Hayat , yanzu kuma ta rabu da su may be rabuwa ta har abada dan ba ta san yadda rayuwar su za ta kasance ba bayan tafiyar ta , kamar kar ta tafi kamar ta zauna tare da su , amma inna da kan ta ta ce ta tafi may be ta ga abun da ita ba ta gani ba kamar Inna ta san abun da ta ke tunani sai ta ce mata " don Allah Meriem tashi ku tafi tun dare bai yi ba , kin san hanyoyin nan ba su da kyau musaman cikin dare " gyada mata kai Barira ta yi hawaye na zubo mata , ta rungume Inna kamar za ta yi kuka ta ce " zan yi kewar ki sosai Inna , don Allah ki kula min da kan ki " Rungume ta ita ma Inna ta yi ta na fadin " ni ma zan yi kewar ki Barira , ki kula min da kan ki don Allah , kar ki yi abun da zai janyo miki matsala kin ga mutanan nan sun ce za su tafi da ke , dan haka ki kiyaye ki ba su girmamawa ko ba komai ta girme ki , dan haka ki ba ta girman ta kin ji ko Meriem ? Allah ya tsare min ki , Allah ya kiyaye hanya ya kare min ke duk inda ki ke " ta kai karshen cikin raunin murya " Inna kenan kin yarda za ki bi mummy , mu koma da ita ? " Hayat ta fada cikin rudu a hankali Barira ta dago da ga jikin Inna ta saki murmushin karfin hali ta ce " Eh za mu bi ta " dan zaro Hayat ta yi ta na fadin " Inna ni ba zan koma ba , wlh cikin gidan akwai wani mai idanun mage , ba shi da kirki ko kadan har shake ni ya yi kuma ya ce zai kashe ni " ba ta gama rufe bakin ta ba Nihal ta bushe da dariya ta na fadin " Hayat , yanzu yaron nawa guda ki ke ce ma mai idanun Mage ? haba sai na aura miki shi ma , ki zama matar mai idanun mage " ta kai karshen ta na sakin yar karamar dariya tsuke fuska Hayat ta yi ta na fadin " ai mummy ba karya na yi ba " ta kai karshen ta na kauda kai gefe kamar ba ita ta yi maganar ba yar karamar dariya Nihal ta yi kafin ta mike tsaye ta na fadin " Shikenan ku tashi mu je , bari idan mu je gida ki tambayi Vedad wanene wannan , na san da ga ranar ko hanya ya bi ba za ki sake bin hanyar ba " mikewa tsaye Barira ta yi , ta riko hannun Hayat ta mike tsaye , su ka yi wa Inna sallama sannan Nihal ta zuba mata godiya da makudan kudade na Franc CFA wanda su ke aiki da shi a Niger sannan su ka baro gidan Barira na fitowa ta ga manyan motocin da Nihal ke tafe da su , ita duk duniya ba ta taba ganin irin su yau a ce ita za ta shiga wannan motar a haka su ka shiga cikin motar Nihal da Hayat da Barira su ka shiga mota guda Already dama Vedad da Iqbal su na cikin motar a haka su ka tada motar su ka nufi fadar mai gari kafin Barira Nihal ta yi kafin ta ce " Na ce , na ji wannan tsohuwar ta kira da Meriem kuma Barira , wane ne sunan ki na gaskiya " wani cool murmushi Barira da ke rungume da Hayat ta saki kafin ta ce " Meriem ne suna na , Kawai dai su na ganin yaunin kiran sunan saboda sunan mahaifiyar mama ta ne shi ya sa su ke kira na Barira " gyada kan ta Nihal ta yi kafin ta ce " Ni gaskia Barira bai min ba dan haka da Meriem zan dinga kiran ki " dan karamin murmushi Barira ta saki kafin ta ce " Shikenan Aunty ba laifi " ( 😴😴😴kun dai ji yanzu Barira sunan ta Meriem dan haka kar ku ga na saka Meriem ku ce wacece duk Barira ce ) Meriem na gama rufe bakin ta Hayat ta dago da ga jikin ta , ta ce " inna idan mun isa Fada don Allah ina son na je na ga Hawa , tun da gidan su kusa ne " Meriem na shirin magana Nihal ta riga ta cewa " Wacece Hawa kuma ? " da sauri Hayat ta ce " Abokiya ta ce , a tare mu ka tasso ina son na je na gan ta don Allah " ta kai karshen ta na marairaice fuska murmushi Nihal ta saki kafin ta gyada mata kai dai'dai lokacin da motar ta tsaya juyowa Felix ya yi kafin ya ce " Sorry madam motocin ba za su iya wucewa ba sai dai mu tafi da kafa " " Shikenan ku sauko mu tafi , Hayat za ki iya tafiya wajen Abokiyar ki , Iqbal zai raka ki amma kar ki dade ki dawo kin ji ko ? " Nihal ta fada ta na kallon Hayat gyada mata kai Hayat ta yi ta na murmushi da sauri Felix ya sauko ya budewa Nihal kofa ta sauko ta nufi motar su Iqbal da sauri Felix ya sha gaban ta , ya bude mata kofar baya inda su Iqbal ke zaune nan ta ga Vedad har ya yi barci ya tada kai da cinyar Iqbal wani cool murmushi ta saki kafin ta ce " Iqbal don Allah ka raka Hayat wajen wata Abokiyar ta za mu je wajen mai garin ba za mu dade ba " dan karamin tsaki Iqbal ya yi ya na fadin " mummy wai yaushe za mu bar kauyen nan , i'm tired " hannu ta kai saman kumatun shi ta shafa a hankali ta ce " sorry my baby boy , sauko ku je ka ji ? " ta kai karshen ta na janye hannun ta da to ya amsa mata kafin ya janye kan Vedad a hankali ya sauko da ga cikin motar dawowa wajen motar su Nihal ta yi inda Meriem da Hayat ke tsaye ta ce ma Hayat " wuce ku tafi kar ku jima " gyada mata kai Hayat ta yi kafin ta nufi Iqbal Nihal kuwa ta yi gaba ita da Meriem Felix da wani guard na biye da bayan su Hayat kuma ita da Iqbal kadai su ka nufi hanyar gidan su Hawa , su na tafe Hayat na ba shi labarin abotar ta da Hawa shi dai kawai ya na sauraron ta ya na sakin murmushi gaskiya abotar su ta tuno mishi ta shi da Vedad , dan duk duniya ba shi da Aboki kamar Vedad karewar zance Vedad ne kadai abokin shi a duniya , duk wani siririn shi Vedad kadai ya ke iya fadawa , duk wata hira da zai yi da Vedad ya ke yin ta ko da kuwa ya san abu me wuya ne ya gane abun da ya ke Fada mishi