[2/13, 7:56 PM] AsmaBaffa: 🏫TANTIRIYA🏫 A GIDAN YARI BOOK 3 ~TAIMAKO~ 1-5 Official By AsmaBaffa SADAUKARWA GARE KI AIDA MAMAN TASNIM PAGE NAKI NE MRS CHIEF *ZINARIYAR MACE⚡* *Wai shin 'yar'uwa menene matsalarki? zubewar nono, ko kuma rashin kwankwason juyawa a falo maigida ya shiririce ya manta da tibi da matan tictok, menene matsalarki ne? rashin ni'ima ko kuma mugun sanyin da ya yi miki katutu, shin rashin taushin fata ne ko kuma kuraje da tabbani, ko bala'in ramar da ta addabeki kuma babu rashin ci ba rashin sha a gidan auranki, gwaigwayewar gashi ce matsalarki ko kuma kaushi da faso na tafin kafa da bushewar fata, kina bukatar fatarki ta yi glowing kalarki ta fita kuraje su mutu, ko kuma kina bukatar azababbun turaruka da humra tare da turarukan wuta. Na san dai kuna da yawa matan da tumbi ya yi musu karan tsaye ina nufin ya katse muku hanzarin yi wa maigida gwalli da muskuce-muskuce a falo😃 Nesa fa ta zo kusa AL-KUTUBIYYA ISLAMIC MEDICINE sun tanadar muku da nau'in magungunan da suke magance kowace irin matsala da izinin Allah. Babban burinmu shine sha'ani na aure ya inganta a samu daidaito. Muna da.* Na gyaran nono. Na sanyi. Dilka tare da hadin sabulu. Duk Wani nau'in maganin mata. Humra turarukan wuta perfumes, original miski tahra 3in1, ciccibi budurwar kaza. Had'addun supplement irin wad'anda ba su da matsala. Maganin Sliming wato narka tumbi. Abubuwan da muke sayarwa suna da yawa, kuma babu asarar dukiya. Muna garin kano kuma muna tura kayanmu kowane gari fad'in Najeria da Nijar har ma da kasashemn ketare. Kai tsaye a tuntu'bemu ta lambobin wayarmu domin karin bayani. *08089965176* *07084653262* Washe gari Khadija wato Mero komawa tayi ta cikin dakin da take kokarin lallai sai ta fasa shi,tana zuwa taji sheshekar kukansa ta bangaren dakin da yake,yau taji wani a kusa da shi tayi mamaki Jin ana bashi hakuri,Yana cewa itace wacce zan aura shike nan ta rasu ta barni,Ido Mero ta zaro tare da dafe kirji da hannu biyu tace dama Yana da wacce zai aura ma ashe,ta rasu Kuma to Allah yaji kanta idan tamu tazo Allah yasa mu cika da Imani" shine yake wannan kukan kamar wani mace sabo da soyayya,shi yasa in ba dole ba me za ayi da me kudi Abu kadan Kuka ba juriyar wahala,talaka kuwa ba ruwansa ya Saba da kaddara iri iri,kasa hakuri tayi da karfi tace to a gobarar ta Kone?Wanda suke cikin dakinsa sun zaci Aljana ce tsoro ya kama su Dan su iya tsayin rayuwarsu basu taba Jin maganar wani ta bayan dakin wani ba bare mace ma. Matashin magana yayi yace ae gobarar har da ita ta Kone,Mero tace sai ka daga Murya banji baaaaa.......tsaki ya ja da gajiyawa yace da karfi da ita gobarar ta Kone,Mero tace Allah yaji kanta tayi Mutuwar shahada,su dai mazan tashi suka yi suka fice basu yarda da mutum yake magana ba. Khadija taci gaba da magana ka gama kukan ne? banza ya mata,kyale shi tayi taci gaba bula katangarta yau dai taci nasara ta bula Inda ya tsage yatsu biyu zasu iya shiga,idonta Daya ta manna a jiki ta leka taga dakin gashi nan dai wai a haka VIP ne,tace wani abin sai gidan yari. Maman Wahida tana gidan yari yanzu Kam ta Saba ta zama Yar gari harkar gabanta take yi,iyalanta suna yawan zuwa dubata bata da matsala a vip take zaune,masu hali basa fadawa matsala,bata shiga harkar kowa indai ba a vip kake ba to tasan baka da gata ko kulaka baza tayi ba. Mero bata San Maman su Wahida kanwar Mima bace tana dai ganinta kamar su daya da Mummy sai ta dinga mamaki, yau dai gaza hakuri tayi ta nufi wajenta da take zaune tana hutawa abinta. Mero tana zuwa tayi Sallama sanye take cikin riga da skirt na wani tsohon Leshi Wanda suma Azima me kwana ba wando ce ta bata su Ganinta cikin tsumma,Mero tace Ina yini,Maman Wahida da kyar ta dago ta Kalli Mero Khadija Shekeke tace ya aka yi? Dan ma kin samu na gaishe ki ,na saki ki gaishe ni? Khadija tace na kwace gaisuwa ta ba Ina yini ba,dama kama kike da wata Mummyn Spark,da sauri ta Kalli Mero tace a Ina kika sansu kanwata ce uwar mu Daya uban mu daya,Khadija tace da Mima,da Rafeeq,Misam duk ba wanda ban sani ba a cikinsu,Sai lokacin tace zauna,Khadija tace uhm da kika ji nasan Yan uwanki to ni ba me kudi bace shara da wanke wanke nayi a gidan Mummyn Spark,Kuma rannan Spark yazo wajena. Maman Wahida tace Spark din yazo wajenki? Mero tace ai shi bashi da matsala shi yake bani kudi da komai,amma ni Ina a matsayin kamar uwarsa ya kasa zuwa mu gaisa,Mero tace laifi kika Masa watakil ai ku halinku sai addua kwana Nan Yar uwarki zata zo ku hadu ku zauna kuyi ta zumunci,Mummyn Spark kwana nan zaki ganta a gidan nan,Maman Wahida tace ubanwa ta kashe ke karki jawo mana masifa a dangi,Azima ce ta fito tana rangwada tace Khadija yau baza kije sakar bane? zanje mana muje to,Khadija ta mike tabi Azima suka wuce Mero tace ke Azima karatun Nan da kyar nake ganewa kin San ni dakikiya ce gwara ma na addini Ashe haka ake wankan tsarki,na dade Ina haukata ban sani ba,ai sai jiya na koya,Azima ta dinga dariya tace gaskiya Jahila ce Khadija,Mero tace ta karshe ma, Gani da suna me dadi me asali amma ban gaji me Sunan ba gaskiya iyayena sun cutar Dani yanzu a gidan yari nake wayewa Kai duniya,ni Kuma a gidan yari nake Ilimi Ina wani zama Yar birni,Azima tace gashi Nan kin koma Yar birni na gyaraki tsaf,rashin kunyar ne har yau baki fara gogewa ba Dan Allah kiyi ki koya ki karasa cika sharudanki na gidan yari,ni kin ganni idan na fita a gidan yari duk Wanda ya aureni ya aurarwa kansa tsiya shi yasa bama na so na fita ni karshe ace nayi aure Kuma ni ba Wanda ya isa ya sani ko ya hanani. Mero tace uhm Azima ke kam ai baza ki fita bama sai kaddara tunda laifinki ba sharri a cikin,Azima tace thank God nayi nadama ni wlh na Saba da zaman gidan nan ko gida na koma ma bazan ji dadi ba,Mero tace gashi mun hadu wai Azima kin San su Chika da Beauty,Azima tayi dariya tace daina tuna min su,ke gidan da kike aiki baki yi dace ba wlh wasu Yan aikin suna dace acan suke samun Ilimi amma suka barki a Jahilarki Khadija,Mero tace su ai Yan boko ne da karatun Boko suke aiki na addinin suna da shi dai dai gwargwado amma sun manta ma kudi da duniya yasa sun manta ma da wani Ilimin addini bare su koyawa wani,sannan duk talaka baida daraja a wajen su ta ya zasu koya Maka Abu suka San ma me kake ciki bare wacce nake gidanta a cikinsu itace ma tafi kowa lalacewa. Azima tace itace Danta yake auren Naila Inye lallai Naila tayi prison mijinta yayi prison ga uwarsa zata yi prison su uku rigis duk prison sai kace gado,Dariya suka yi Mero tace gashi nima daga zuwa aiki gidan na fado Ina tsoron Naila karta haifo Dan Birsina,karasawa suka yi Inda ake koya musu sakar,Azima ta wuce bangaren nata ta kayan Sanyi ita kuwa Mero bangaren mificin sarakuna irin na fadar sarki masu kyau da tsada su ta iya,tayi mugun iya saka su tunda tazo ta koya,gashi in sun saka baza a basu kyauta ba sai dai ka siya in kana da kudi,Mero sai da ta siyi biyu wai sai ta yi kyauta. Bangaren su Malam Jilani suna zaune Dan Indo ya shugo idonsa jajir yace kai akaramakallas gaba dayan ku Jiya Mafarkin Jamilu nayi ya dawo gidan nan,Malam Garzali ya tuntsire da dariya yace wai Dan Allah baza ka manta da Jamilu ba,tayi aure ance tuni,Dan Indo ya jawo tarkacen kayan Naila data bari ya kalle su,ya daga wani katon bujen wandon ta ya furta Allah sarki duniya yanzu wannan Jamilu ta saka shi,Malam Jilani Yana boye dariyarsa yace Matar wani ce dai yanzu,haramun kake aikatawa,Dan Indo yace Allah ya tsinewa yaron nan Spark,zuwansa ba alheri bane ya cuceni,yanda nake Son Jamilu na tabbata baya sonta haka,duk sanda na sake ganinsa a gidan yari ko ziyara yazo sai ya yabawa Aya zakinta,Malam Jilani suna ta dariya,Dan Indo ya sake Jin Haushin su yace ai kune manyan munafukai dama karya kuke Kun San macece shi yasa kuka riketa a dakinku,Kuna fakewa da karatu Yan iskan banza Yan iskan wofi,Malam Sharu yace mu mene namu a ciki yaro dai Jamilu da hannunka kayi Masa hanya ya bar gidan Nan sabo da haka laifinka ne,mu karatun mu muke da addua,ai ba karatun Allah kuke ba ya ja tsaki ya fice. Schola ne ya tare Dan Indo yace ya akayi ne Dan Maza? Dan Indo yace jiya mafarki nayi Jamilu ya dawo gidan nan,Schola yace wai Jamilu Terror? yace ae,dariya Schola ya dinga yi yace tab sai akace Maka gaskiya ne sannu waliyyi to Kai da Jamilu har Abada tana can tana ta Shan madarar Nido yanzu haka ma an samu Rabo ka samawa kanka lafiya ka hakura,Kaga ni na tafi wajen kawata Khadija nasan anjima kadan zata bayyana a Jikin katanga mu Sha hira Ina dalili ka likewa mace daya,Jamilu ai ya zama old version,ga new Version latest Khadija Ina laifi kana Jin Muryar mace ma a'a mu munyi can" ya wuce yana rangwada. Wata Majalisar ce guda suke kafata a wajen sabo da Mero tana zuwa ta Jikin wajen suna Jin Muryar mace,Mero da Azima suka zo ta wajen Mero ta kwala da karfi Salamu Alaykum harda rige rigen amsawa,Goje yace Kai Muryar mace duniya ce wannan yarinya Allah ya mata albarka tana kwantar min da zuciya tana sani nishadi,rabon da naji Muryar mace tun Jamilu Tantiriya tana nan,Mero tace Kai Yan Maza har naji warin ku na gardawa ta nan,irin na ubanki cewar wani me Suna Balarebe,Mero tace Ubana Yana can Babata ta takura Masa shine ka zage shi ai abin yayi Masa yawa Allah ya isa,Ina ma zaki iya shugowa gidan nan bangaren mu,Mero tana dariya tace uban me zan muku in na shugo,Schola yace madarar Nido za a Baki iri iri harda me bulkodi ahayye ni dai Allah ya tsare ni neman Yar uwata mace,Mero da Azima suna ta dariya,Azima tace wayyo gashi bana kwana da wando,Goje yace ku jefa ni ciki Dan Allah,I love you a jefa ni ciki,Hanif ne yazo wucewa ta wajen yaji suna ta ihu da dariya,da izzarsa ya dan tsaya yaji Muryar Khadija ta daki dodon kunnensa tana cewa a gidanmu ga shimfidita ga Kaza taka kyankyasar 'ya'yanta a kauye,ni fa a birni na koyi tsafta a gidanmu sai mu gama wanke wanke mu wanke kafar mu da soson wanken Kwanon,su Goje suna ta dariya sabo da Fadi ba atambayeka ba din da Mero ke yi kullum sai ta fada musu abinda suke yi a gidansu na kauye. Balarabe yace tab Allah yasa bakwa abincin siyarwa,Mero tace cab ai kuwa wallahi muna yi awara da Koko,tsohon dankwalina babata ta dauka da shi take tace gasarar Koko da awara,har skert dinta na ciki mun taba amfani da shi,Schola yace wayyo kunya ku matsa na boye kaina ni Schola Ina zan sa kaina Yar uwa tana ta bankada,Goje yace to ke Khadija baki da kanne ne? Me kace bana ji sai kayi da karfi,da karfi yace Baki da kanne? Mero tace daga ni sai kanina Yana kauye wani Dan banza shashasha nake ganinsa yanzu Kuma a haka sai kaji watarana wata har kasa bacci zata yi a kansa Allah ya kiyaye wacce taso kanina Muneer tayi asara,Azima tace ke muje dalla lokacin makaranta Kinga ke kike koyon Addini muje ko Kya samu ki daina wannan iskancin zancen naki,Dan Allah karku tafi cewar Muler muna Jin dadin mu kamar mu rungume ku,Mero tace wayyo Dan ma Baku ganni ba,Goje yace Allah? tace Allah da kunji a cike muke kamar ana bamu kaji,Goje har da dafe Kai yace Kuma fa da gaske ne Yana magana da sauran mazan,Hanif kallon su yayi kawai wani takaici ma ya kamashi mene abin dadi a nan,yace gaskiya ku Baku San ma mene abin dadi ba,Goje yace Kai ai sabon zuwa ne baka wani Dade ba shi yasa kake fadar haka da ragowar turirin mata a jikinka ka shugo bai gama barin jikinka ba shi yasa,ka kyale mu Muji dadin mu,Hanif yace Goodluck,Yana kudu Dan uwarka Yana Niger Delter, Goodluck ma ya sauka daga mulki karewa cewar Schola Yana ta faman cakaki,yace tun yaushe nake binka Ina naci Ina sonka ka zama budurwa ta kaki yarda wai Kai me tsafta shine yanzu zaka zo ka takura mana, Kai kudin naka ma ba kyauta kake ba, tunda kazo gidan Nan sai girman Kai sisinka ba Wanda ya taba ci,Hanif yace Allah ya kiyaye irinka Dan neman takashi yaci kudina,taka dai da alama baza tayi haske ba tunda dai ba irin mugun farin nan bane Kai ato farar takashi sai Spark,dariya Hanif yayi yace ko waye wannan Spark din oho da an tashi gori da shi ake kwatance. Sai dare Mero ta gama surutunta zuwa dare ta koma dakin da bama a shiga Inda ta fasa,Hanif an kawo Masa take away hadadde da nama Yana ci Yana ta jira yaji muryarta sabo da da ta Saba zuwa Yana Jin surutunta Yana samu Dan sauki a ransa,sallama tayi ya amsa da kyar,tace me kake ci ne? yace nama,masu kudi Allah ya Kara budi,Ameen ya furta yace ba waje da na San miki,tace ga kafa dinga sako min Yan siri iri ta wajen zanci haka,yace to ya mike ko wanne Yankan nama sai ya raba shi gida uku ko hudu sannan ya samu ya Dan turowa Mero kamar wata tururuwa ta karbe ta cinye Kuma. Naila ce ta fito tana rike da mara tana Nishi ta samu Spark a palon sama Yana kallo tace wash Allah Baby wayyo marata,zan mutu ta durkushe a wajen tana murkususu,a firgice Spark ya mike ya rike Naila yace me ya faru? Yanzu naji ciwon mutuwa ne wannan, Spark ya rude ya dauketa da sauri sauri suka tafi asibiti,Naila tana kuka tana bige bige a mota da kyar ma ya iya driving. Suna zuwa aka karbeta aka fara bata agaji,sai da aka Dade Sannan mace Likita ta fito ta samu Spark hankali a tashe Yana jiran amsa meke faruwa. Likita tace Sir Alhmdllh taji sauki amma kayi hakuri ciki ta samu baifi 4weeks ba Kuma ya zube,Spark yace ke likita ance bari yafi nakuda azaba kalau matata take? Indai matata kalau take shike nan Dan ciki taje gobe ma nayi sabo,dariya ya bawa likitar tace kalau take yace to Alhmdllh nan da jibi ma zan mata sabo Inshaallah,yanzu me ake bukata? Likita tace ai tafi karfin Pad sai dai pampers babba ake siyawa matan da suka haihu ko bari,Spark yace ban gane ba nufinki yanzu Jinin jikinta zubewa yake baku da hankali kuka ce kalau take,Likita tace ya gama fita cikin amma ai dole zata danyi jini kafin a samu ya dauke a hankali duk abinda ya dace anyi,Spark yace nifa shi yasa bana son matter din Nan ta ciki-ciki,ya fita yaje ya siyo abinda tace ya kawo mata,ta bawa nurse Dake asibitin kudi ne ko ba Yar jinya akwai masu yi. Naila jikinta ta gyara ta shirya ya kawo mata wasu kayan ta canja ta fito kamar ba ita ba fes,waccen kayan Kuma data cire sabo da wadata sai tace ban taho da me wanke min ba ni na bar miki ko ki zubar,sai da ta fito Spark yace Ina kayan da kika cire? Ni wlh bazan iya wankewa ba na barwa nurse in bata so ta zubar. Spark yace kut kayan da nake so nace dinkin Yana miki kyau yau fa ni nace ki saka su shine kika bayar wlh ba Yar iskar da zata saka,Naila tace sun baci fa sosai,yace ma wanke,sabo da baki San zafin nema ba in siya miki Abu me tsada kice a zubar kin San nawa ce atamfar? Kudin banza gareni,Naila kuka ta fara Dan kar a karbi kaya tasan halinsa ba kunyar uban kowa yake ji ba,kaina Yana ciwo kana ta min fada,Spark ba yanda ya iya yace sorry muje amma indai naga Nurse din nan sai na kalleta tunda ta sa min kaya ta shiga uku kurwata baza ta kyaleta ba,Naila tace ka kalleta Kuma? Tace kwarai ai asibitin nan sun shiga uku sun dinga ganina kenan,juyawa Naila tayi ciki da sauri tace Nurse kiyi hakuri ki bani kayana mijina yace bai yarda ba,Nurse tace ba komai gasu ma an zuba su a Leda in kinje gida Kya wanke,Naila ta karba ta koma mota a boot ya saka ledar kayan suka tafi gidan da magungunanta,suna zuwa gida ya bawa me aiki yace a wanke su tas in anyi normal da hannu a zuba su a washing machine tace to tana ta yiwa Naila sannu gata babba dama tasan komai Tana gamawa ta hadawa Naila ruwan wanka ta gasa jikinta tayi wanka sosai tare da gyara kanta sannan tazo tayi kwalliya cikin wata fitted gown ta Leshi brown,abinci taci ta koshi Sannan ta Sha magani ta kwanta ta hau kiran waya Hello Ana gaisawa zata ce wlh bari nayi yanzu amma da sauki Alhmdllh mun dawo gida, kowa sai da ta fada Masa tayi bari,Spark ma haka har da kiran Mima yace Naila ce tayi bari, subhannallah Kuna asibiti yanzu? ai Abin yazo da sauki kalau take muna gida,to bari muzo cewar Mima. Kafin wani lokaci gidan Spark ya cika da Yan Uwa su Chika,Ikhram duk sunzo,Naila ita barin ma sai murna take kamar wacce ta haihu,sai dare daga Chika sai Ikhram a gidan,Naila tana tsakiyar bed suna ta hira Spark ya shugo bedroom din,zama yayi a gefen Naila ya kalleta dariya ta bashi yanda take faman murna tayi bari,Chika tace wai korar mu zaka yi ne ai ka jira mu tafi kana babban Yaya Sam baka yin yayan Kai,Spark yace wai Yaya manya da wa zanyi wani Yaya wannan Dan iskan mijin naki da ya fini duniyanci,Arham ne ya shugo yace Chika ance ku fito na kaiku gida,Aunty ya Jikin? Naila tace Alhmdllh da sauki,Spark ya kalla yace Yaya Allah kawo wani da wuri,Spark yace a'a ba yanzu ba ai yanzu sabon Ango zan dawo,Naila ta zaro ido,Chika tana jinsu tace Kai Arham dan Allah muje"tafiya suka yi,Naila tace bari nayi wanka Yau bacci har da makara,Murmushi Spark yayi tare da furta zaki murmure ne dole na kwalbe,Naila yau dai bani da amfani ba mamora a jikina sai ayi hakuri Kuma,Spark yayi murmushi kawai. Annoor kuwa Iman tunda ya samu ta dawo sai da ya lallabata da asuba ya sake Kwalbewa,Iman duk tayi zuru zuru da ita,abinci ma sai daga gida ake kawo musu ai kuwa ta Sha Allurai shine samun saukinta ma. Iman yini tayi a kwance Bata iya tafiyar kirki sai zuwa yamma da ta Dan ji sauki,mayen Yana gefenta kamar zai cinyeta tace zan danyi tafiya dan Allah ko naji sauki,Annoor ya mike Yana murmushi abinsa shi duniya sabuwa,hannayenta ya rike a hankali ya mikar da ita tsaye harda cewa sama da ikon Allah,dariya ta fara tana dukan damtsensa Shima dariya yake cike shaukin so,ya riketa Yana koya mata tafiya a hankali,Hannu ta yarfe tana cije lips yace daure,ture shi tayi tana murmushi ya fada Saman bed,fadowa tayi kansa tare da sakin Kara,yace sorry tashi aci gaba ya sake riketa suna tafiya a hankali Yana ta faman tsokanarta,yace wai Ina Sunan da kika Sa min na love kin daina fada yanzu,Iman tace ai yanzu ranka ya dade kake wa zai ja da Kai,me gida ran gida baki aka fiku ba aiki ba,kune gaba da mu,yace wash Annoor ka kashe ni,murmushi tayi tace ka daina please,gwara ma ki bar fadi bazan daina ba. Bangaren Nabeel kuwa shi jinyar Yar matarsa yake sosai kuda baya so ya taba ta,sai bakinta da ya bude sosai tun a ranar surutunta ya baci bata shuru Hidaya,ita first night din kamar an bude mata baki. Naila ce ta kira Umma ta sanar mata tayi bari,Kubra tace Allah ya sawake ya kiyaye gaba,tace Ina Abba? Zaraf Abba yace gani Ina jinki bari kika yi Ashe to Alhmdllh yafi babu akan ace ko bari bata taba yi ba gwara ace ta taba bari ai Kinga ana sa rai,Naila tace hakane Abba kamar Dan kadangare,Abba yace ke Zubaina sati hudu ai jini ne Ina ya zama kamar kadangare din,Naila tayi dariya tace ai a haka na gane,Abba yace a'a ba da bane gaskiya gudan jini kika gani idonki ya rufe,Kubra tana jinsu Abba yace tunda lafiya kike ai anyi arziki duk wata karya ki ajiye abarki gefe Naila Allah ya baki wani ni kaina na matsu naga kin min jika wlh ki dage tun kafin Dara taci gida na fara miki gori da kaina don kuwa na gaji da Kara da kawaici na kusa fara gori,Naila tayi dariya tace Abba da kanka,to ni dai Kinga na haihu bare ace tunda nayi gori hakki ya kamani bazan haihu ba Nima da yarana,na kusa gajiya zan fara yi muku gori ke da mijinki,Naila tana dariya tace Abba Yana jinka. Ta zaci Abba kunya zai ji sai yace bashi wayar ma,ta mikawa Spark Dake gefe Yana dariya Yana Jin Abba,ya karba suka gaisa, Abba yace wai Kai aiki ne yayi Maka yawa ne? ya kamata ka dauki hutu ka samu nutsuwa ance rashin hutu ma Yana hana haihuwa,na gaji da halinku ka zauna ka binciki Naila Anya ba wani Abu ta Sha ba Bata San tana da ciki ba ta gantalar da shi,Spark yace to ya mike zai bar wajen Naila ta rike shi Kam tace wlh ban yarda ba a gabana zaka gama wayar Nan ka karo volume,Spark yaki karo Volume tunda ya rage volume sai da ya gama wayarsa sannan ya kwanta abinsa a gefenta Yana tambaya yau tun safe me da me kika ci?Naila tace abincin da Kaci,wato Abba ne yace ka tambaye ni ai na gane ka. Washe gari Abba ya bude shagonsa na kayan masarufi harda tiles yace saura katifa,takanas ya siyo katifa Yar Siririya ta Yan makaranta ya saka a can gefe kullum Yana Kai ko a zaune ko a kwance kowa in zai wuce Yana kallonsa ai ta sheka dariya shi kuwa ko a jikinsa yace kanku ake ji bazai yuwu Basir ya kashe ni ba akan Ina so gidanku a tuka tuwo sai dai idan kar a siyi Masara ta. Rafeeq yau Mima yaje gaisarwa ya samu Arham gososo yayi matashi da cinyar Mima,Rafeeq yace Kai mene haka? Arham yace Kai kaje ka hau ta matarka mana ai kana da ita ni ka barni na hau ta Uwata ni wlh Mima da zata ci gaba da shayar Dani tsaf zan koma baya,Mima ya kalla yace Dan Allah ki Sha ruwan kaikayi su kawo,Rafeeq yayi dariya yace to ke Mima kinji danki shi yasa ya Raina ki Kinga irinta,Mima tace Kai dalla rufe min baki sanda muna talaucin mu kazo ne gudun mu kuka dinga yi sai yanzu zaka dame mu,Arham yace ai yayi mata yanzu ya daina lagawu da baki wlh da a baya ne da yanzu ya mana batsa,Dariya Rafeeq yayi yace yanzu kuwa nake batsa yaro kawai dai an daina yi a gaban ku baku da kunnen ji me kunnuwan ji tana gida,Arham yace muna ji mana me zai Hana ai mu muna Jin dadin wannan batu,Mima tashi tayi ta cire takalminta ta Kifa Rafeeq da gudu tana zage zage,Rafeeq ya shige bedroom tace zo ka tafi gidanka wlh,Mummy tana zaune tana faman kallon takadar sammacinta ta kotu,Arham ya kalleta suka hada Ido bakinsa ya danne da hannu Yana faman dariya,Mummy ta kalle shi tace Kai dan Uwarka da wa kake? Yace ba fa dake nake ba ni,wai Ina Alhaji Baseeru ne? Ina ma kin samu ciki abinki,Mummy tace Dan iska shege ba Yana can Dan wahala,kamar ni zanje bikonsa don a San ya za ayi ko wani auren nayi na fito ya sake aurena wai shi a baya ma kaddara ce dama na Masa tsufa Mamansa ce ni,Arham ya boye dariyarsa yace gaskiya bashi da mutunci duk garar da ya kwasa,Mummy tace ai ya manta,Dan Adam butulu cewar Arham,Mima ce ta fito tace kin biyewa Arham kina Hira Yana ta zurma ki wannan yaran akwai na dauka ciki tashi kaima ta fatattaki Arham Shima. Shaheed ne ya dawo Yana shugowa tace juya kasan Inda dare yayi Maka,me nayi Kuma ni daga dawowata school fa naje,Mima tace kasan Allah wlh zan fadawa Papan ku,ka wuce part dinku kawai bana son magana,Mummy tace yawwa haba yara duk sun addabi mutane,Mima tace wlh ni da zasu samu mata ma duk a musu auren yafi min ai sun Isa,Shaheed ya fara murna Yana Shoky ahh Shoky ai bamu sani ba ni wlh a daura ma data Annabi,ko wace a bata ni sadaka 9mnths sai jikoki ta ko Ina,Junior ne kawai Bai Isa aure ba cewar Mummy,Shaheed yace ku bashi yarinya ku gani a kulle su a daki wlh sai ta haihu,Rafeeq ne ya fito yace daga zuwa gaisuwa ni ku tsaya na fice na tafi ya lallaba ta gefe ya fice,Shaheed ma ya tafi abinsa Yana murna ance za a musu aure. Hanif Usman Dan asalin Adamawa ne,Fulani ne gaba da baya,tun Yana dan 3yrs Babansa ya rasu sai mahaifiyarsa a gabanta ya taso ya girma ta tsaya Masa yayi makaranta har masters a kalla zai Kai 33yrs,kyakyawan matashi ne na gaske,fari ne amma ba irin Kal Kal ba,Yana da dogon hanci,bakinsa dan daidai ne me kyau,hakoransa masu matukar kyau haka idanuwansa,Yana da yalwar gashi baki wuluk me kyau,shi bai cika tsayi ba Kuma dole a kira shi da dogo,komai na Hanif me kyau ne,haka gashi ko wanne sutura ya saka sai ya zuba kyau ta amshe shi,baida hayaniya sannan ba a fiye fada da shi ba kawai harkarsa yake, har Mamansa ta auri kanin babansa suka yi Yar gida,bayan Alhajin nasa Yana da mata da yaransa biyar amma duk mata ne Kuma duk an musu aure a yanzu suna da yara ma ko wacce. Hanif tunda ya taso yake da kashin arziki Ya fara aikin gomnati Yana kasuwanci sai kasuwancin nasa yazo ya danne komai,kudin da yake samu har da na hauka ma Allah ya sa Masa Albarka,Yana da kudi matuka sosai,Business dinsa yafi karfi a Kano state a Nan ya kera gida na karshe a GRA Yana zaune shi kadai iyayensa suna Adamawa da dangi,Yana da kadarori sosai matashin me kudi ne. A Yan uwansu Adamawa akwai wata Khairat wacce Alhaji kanin babansa ke riketa,tun tana karama Hanif yake son Khairat kamar ransa,wacce Kuma a sanadin gobara data kama gidan Umminsa wato gidan kanin babansa tayi ajalin Khairat wacce ya Sha kuka kullum a cikin damuwa yake sabo da ita. Dalilin zuwansa prison kuwa a cikin Yan uwansa ne bangaren Umminsa mahaifiyarsa ta samu Dan gidan Yayarta wacce ta Dade da rasuwa ana ce Masa Sudeis zai Kai 25yrs ta turo shi Kano wajen Hanif akan zai koya Masa business zai Maida shi yaronsa,kaddara tasa satin Sudeis biyu aka neme shi aka rasa daga fita kasuwa ba a sake ganinsa ba,Hankalin Hanif ya tashi matuka sabo da a gidansa yaron yake zaune Kuma wajensa aka turo shi,dangin uban yaro suka ce baza su yarda ba dama Hanif Dan mafia ne kudin mafia yake da su matsafi ne,iya nema da cigiya an rasa Sudeis,Uban yaro ya Kai Kara bazai yarda Wanda aka kama Hanif aka tsare shi a prison bangaren Wanda ake tuhuma ana sauraron kararsu,Alkalin ma nasu yayi tafiya yaki dawowa shi yasa har yanzu ba a yanke hukunci ba,Yana Nan a ciki shima kamar Mero basu San zaman da suke ba. Umminsa da Alhaji suna zuwa ko yaushe sannan Hanif abinci me tsada ake kawo Masa kullum,haka sutura da komai nasa classic ne,kana ganinsa kasan babu maganar wahala a tare da shi,shine Kuma Wanda Mero take kallo a TikTok tana sonsa. Khadija Sani Uba Mero kenan Yar kauyen Kano ce cikin wani kauye dake Danbatta,Khadija su biyu Iyayensu suka Haifa,Khadija itace ta farko sai kaninta Muneer,Babar Khadija Bata da tausayi gata da masifa kamar me Wanda ba boka babu Malam ta mallake mijinta sai abinda tace kasancewar Sani shi wani gashi nan ne dai sanyin Hali ne da shi sai abinda aka ce da shi,duk Inda akace Yayi to Hakan zaiyi kuwa,bashi da gidan kansa,Yana kallo tana cutar da yaransa ba karatun addini bare na Boko sai talla da aikatau baya so amma bazai iya magana ba,komai tace an gama kawai. Gashi duk Inda zata je kamar jaka sai tace sai ya rakata idan da kayan shi zai daukar mata har Inda zata je kawai umarni take bashi,Kuma shi zai fita ya Nemo,banbancinsa da su Abba Dolo shi Yana da zafin nema amma Kuma sai abinda aka ce da shi,matarsa Hajiya Jummai ta hanashi rawar gaban hantsi ga masifa,su Khadija haka suka taso suka ga tana yiwa ubansu,taci kwalarsa ta zazzage shi ba abinda zasu iya. Yau ma gidan ya shugo ya Kai wani gero kasuwa Yana dawowa ya fito da kudin ya zube mata a gabanta yace gasu ki duba kiyi abinda ya dace ni na dauki dubu uku ciki,Baki ta bude ta ajiye tire din dake hannunta gata kyakyawa da ita sai masifa,tace ban gane ba akan wanne dalili zaka dauki dubu uku zube ka dauki dubu daya ta isheka,Muneer Yana zaune Yana cin tuwo yace haba Inna mutum da amfanin gonarsa ya siyar duk ya Baki kudin akan ya dauki dubu uku shine zaki ce bazai dauka ba,Kai rufe min baki ko nazo na taka wuyanka,Sani Wanda suke kira da Uba yace kyale a bata Muneer ba komai dubu dayan ma ta isheni" ya dauki dubu dayansa kawai ya koma dakinsa ya kwanta. Zuwa yamma ta fito zata je gidan suna ta gama shiryawa tace Sani fito ka daukar min kayan barkar nan muje,haka ya fito ya karbi Yar ledar suka fice da yadinsa brown ishirunka maraya,ita Kuma ta Sha atamfa blue da hijab,suna tafiya suna Hira sai kace wasu matasa,abinda take so ita kenan duniya ta San ta mallake mijinta sai abinta tace,ana ta gulmar su ita kuwa tana Jin dadi,yace yaushe zamu je wajen Khadija ne? tace sai an siyar da Masarar da zata zo kwana nan,kasan kudin mota tsada rayuwa tayi tsada. Yace ke da yarki kamar ba ke kika haife ta ba,fuska ta bata ya ja bakinsa ya tsuke Yana tsoro,nesa da ita ya matsa Yana tafiya tace dawo wannan hanyar,yace ta Nan tafi sauri mubi ta nan,to bazan bi ba ta nan nake so" haka ya dawo Inda tace suka ci gaba da tafiya. Yau abokin Sani ya gaji ya sake dawowa har gida ya kira Sani,yace gaskiya ka canja hali abinda kake yi Sani a garin Nan bai dace ba Sam,ace mace ta Maida ka kamar Rakumi da akala wlh mu Maza bama Jin dadin Hakan Sam,ka duba yau fa wai gidan suna ka rakata,Sani fuska ya Bata yace Dan na raka matata laifi ne? Shi yasa ku mutanen kauye har kullum Jummai take fada min na fita sabgar ku baza ku waye ba,tace dama na daina kulaka nine na nace nake Maka alfarma,amma mene aibun Hakan? Ko Jummai ta fada min tace a Makkah ma haka ake yi karewar garin addini kenan haka Maza suke wa matansu,to Kai Sani Balarabe ne ko al'adarmu Daya? Koyi nake da su karku dameni Kuma duk Wanda ya zageni ko yayi gulmata da gulmar Iyalina ban yafe ba,Abokin Sani ana ce Masa Malam yace yanzu yau fa har hannu ka rike mata a titi haba yara suna kallo ba tsari,matar tawa Dan na rike mata hannu koyi nake da Larabawa ko a gaban yarana na cikina zan rike mata hannu,baya ga haka ma ba yin kaina bane itace tace na rike mata shike nan bazan yi ba sai na watsa mata kasa a Ido. Tayi min komai na gidan ta tuka min tuwo na ci da yarana Dan kawai tace rike min hannu Sani sai na kasa sabo da ni Dan iska ne ko me? Ko a garin Fir'auna aka haife ni,karku sake shiga harkarta da iyalina,gaisawa dai mu gaisa amma Banda shiga lamarin auratayya ta,gaisuwar ma ba dole In Kuna ganin da matsala ku kyaleni,amma ni sai me Dankwali sai abinda Jummai tace yawwa. Malam yace Allah ya ganar da Kai,yace Ameen ya shige gidansa Yana shiga gidan ya kwashe zancen ya fadawa Jummai,Jummai tace ai na Dade da fahimtar Malam munafuki ne rabu da su makiya mahassada. Chika tana zaune a Palonta ta mimmike Misam Yana mata tausa sabo da tana da ciki,sai langabewa take tana Nishi,Me unguwa Maman Chika da Baban Chika mahaifi ne suka zo,Chika tayi mamaki babu Sanarwa,Misam ne ya bude musu kofa suka shugo Sanyi da kamshi ya daki hancin su,Chika tana ganin Me unguwa ta hade rai tace me ya kawoka gidana,Abban Chika yace Suhailat bana son shashanci ki nutsu,Misam gaida su yayi a mutunce Yana musu sannu da zuwa. Chika ta zauna ta hade rai ganin Me Unguwa,Mamanta ce ta kalleta ta Harareta sannan ta gaishe su ta mike taje ta kawo musu kayan Sha da ci tace kar wannan ya sake ya Sha min lemo na,Kin San Allah zan Saba miki me yasa bakya ji ne,Misam ne ya mata rada yace calm down su Abba ne fa,Abba ne yayi magana yace dama Me unguwa ne yayi nadamar abinda yayi yazo baki hakuri akan ki yafe Masa,bazan yafe Masa ba kuwa sai dai a bar shari'ar nan ayi ta a gaban Allah. Abba ne ya share Suhailat ya Kalli Misam yace Kai nasan kana da hankali,Suhailat da kake Ganinta bata Jin magana,ni na haife ta amma nasan halinta sarai,lokacin Ina auren babarta Ashe Me Unguwa tsohon saurayin Maman Suhailat ne" to ni ban sani ba Ashe haushina yake ji na kasa shi na aure Masa budurwa,tunda na aureta ta haifi Suhailat yarta ta fari kenan muna zaune lafiya ashe me Unguwa shi kullum budurwarsa tana ransa burinsa ya kashe mata aure ta fito ya aure ta. To bayan Suhailat ta girma ta Kai 13yrs Bata sake haihuwa ba,da ta samu ciki sai bari,Ashe Me unguwa ne yayi mata asiri ake zubar da cikin bamu sani ba,karshe da yaga dai baza ta fito ba sai ya hada baki da wani ya bashi kudi ya shiga dakin matata da dare lokacin tana kitchen ni Kuma na shiga Ina shiga na iske Kato a kan gadona na sunna a tube zigidir,kuskure na banyi bincike ba sai na saketa saki uku,ta koma gida katsina kenan Inda Me Unguwa suke dake duk unguwar su daya,da Suhailat ta tafi,cikin ikon Allah data fito shima bai aure ta ba sai ta auri wani,daga Nan ya fara Jin haushi Yana binta da sharri,ita Kuma Suhailat haushinsa take ji Yana son uwarta tunda taji Labari. Ganin bai samu uwa ba sai ya dawo kan Suhailat tsofai tsofai wai ita yake so,tayi tayi ya daina kulata yaki,sai sharri ma da yayi mata duk abinda ya faru sai yace Suhailat tana ciki,Kullum tana wajen Yan sanda,karshen sharri wata yarinya aka tsinta a bola an mata Yankan rago,me Unguwa kiri kiri kiri yace yaga Suhailat da idonsa da mutane sun sauke yarinya a mota karama,ya kira Yan sanda ya bada rahoto kawai bata San zance ba aka kamata Kuma ya dage da hadin bakin wasu dattawan na unguwa tsofaffin banza sai da aka kaita gidan yari bada hakkinta ba,sharri ba Wanda baiyi mata ba,yaje ya bada shedar zirrrr a kotu,gashi yanzu Yana dana sani da nadama,Misam Yana gama saurara yace ahhh da gaskiyar Suhailat a bar sharia sai a lahira Me unguwa ya dinga rokon Suhailat da kyar da lallashi Chika tace ta yafe Masa a haka ma dole aka mata,Maman Chika ta furta idan Allah Bai baka abu ba duk duniya ba Wanda ya isa ya baka,Me unguwa ka cuceni ka kashe min aure Kuma da na fito ban aure ka ba shine ka koma kan 'yata itama Allah baiyi ba sai da ka kulla mata sharri,wani mutumin babu amfanin saninsa a rayuwa wlh,Me unguwa kansa a kasa yace a yafe min sharrin shedan ne inshaallah zan gyara Halayena,Misam shi dai tunda yaji ance ai ya taba cewa Yana son Chika sai haushin Me unguwa yake ji ya matsu su tafi,Chika ya kira bedroom ya bata hijab yace ungo saka ga tsohon saurayinki nan matsiyaci Dan iska tsohon banza tsohon wofi,ai a haka zai kare rayuwarsa azzalumi wlh na tsane shi tunda yace Yana sonki ni da shi gaba har mutuwa,Chika tayi dariya tace Dan ma baka sani ba lokacin ya zaci bani da wayo naje wucewa watarana ta kusa da gidansa da dare ya taba min duwawu,ai kuwa na saka kuka naje na Kai kararsa sai da aka mana tsakani. Misam ya rike baki yace fyade zai miki ai da haka ake yin fyade ni kiyi sauri su tafi suma su mama mene na zuwa da shi ko ta waya ai a yafe Masa,Hannunsa taja tare da dorawa a Saman cikinta tace kaji babyn mu,Murmushi yayi tare da shafa cikin yace ko mace ko namiji Allah yayi albarka, suka fito suna zuwa palon Misam yace ai Mama da Kun sani ma ta waya kuka kira sai a yafe Masa ko kuzo ku kadai ba sai da shi ba,gwara dai da muka zo yafi yana ta binmu Yana bada hakuri,Misam haka ya kaisu har wajen Mima suka gaisa suka ce tafiya zasu yi harda sauri siya musu ticket din jirgi sabo da kar ma ace dare yayi zasu kwana,da dai iya Iyayen Chika ne ba matsala,Yana kaisu airport bayan sun tafi ya dawo ya iske Haly da Mufee wai sunzo zasu kwana. Misam yace me kuka ce kwana? Muna gari Daya ga baki ga hanci" to ba a nan ba ku koma gidan ubanku, Nan ba waje ko Ina a gidan nan lungu da sako sunna muke yi,munafukai haka kuka ce ba bikina kuke yi ba ku anko ma na Rafeeq kuka yi ku tafi gidan Malama ku kwana,Chika tace haba My Prince,yace ba ruwanki ku tashi ku kama gaban ku bana tsarki ba na hanya,Haly ta mike Mufee ma haka suka fice ,Chika tace me kayi kenan Hakan? Misam yace duk naji maganganunsu sun dawo kunnena ki kyale su kawai ko Mima baza tace komai ba,in sun gyara halinsu sai mu shirya. Suna fitowa Haly tace ai da kunya mu koma gida muce an Kore mu,Yaya Rafeeq Kuma in kaje ma ya dinga wani cin magani kenan,Mufee tace cikin kwanciyar hankali mu tafi gidan Naila tunda tayi bari muje kawai muce aiki zamu dan dinga tayata,ai kuwa can suka nufa sai kace dole,Suna zuwa suka same su a Palo sun saka kana Nan kaya wasu silk silver iri daya riga da wando,na Naila na mata na Spark na Maza,ba karamin kyau suka yi ba,Naila ya aika yace je ki kawo min wayata,Naila tace na gaji wlh Baby sai juyani kake yi yanda kake so,yace to na taba cin bashin ki ban biya ba? tace a'a,yace na hanaki ci Sha da sutura? tace a'a,yace ya batun Kwalbewa? tace Nan ma zam zam,kin taba cewa na baki abu na hana? tace a'a,yace ki taba bani sisinki kyauta? Naila tace Ina naga kudin baka,yace to ta ya bazan juyaki ba,Dan ma kin rainani ne Ina kyaleki shi yasa kike fadar haka,in wata ce jiki na rawa zata yi kafin nace anyi duk da kema kina kokari,Naila tace karfa ka manta Nima Yar gata ce a wajen Kaka,Inda na girma ban San babu ba duk abinda nake so shi ake min,Kuma Allah ya bamu rufin asiri bare kace kudinka na bi ato kana min zan maka,Kai kasanni wlh ko so kake na dawo Maka Naila ta ne ta farko,dariya yayi yanda take zazzare Masa Ido,yace kwana biyu ai kina Off ban saki a corner ba shi yasa kike haka,Naila tayi fari tace na saka dai a corner badan Ina tausaya Maka ba sai na Maida Kai Baseeru na Kone ma ruwan jikinka,dariya Spark yayi sosai yace Allah ya baki lafiya wlh na daina tausaya miki,Naila da kuri tace ni dama bana so ka dinga daga min kafa, a yini a kwana digir digir zaka gani...su Haly ne suka yi sallama tare da kwankwasa kofa,Naila ta ce Spark tashi ka bude kofar nan murmushi yayi ya jawota ta fado jikinsa"kissing dinta ya shiga yi a lips sannan ya mike ya bude kofar ta tafi dakko Masa wayar. Haly ne suka suka shugo da fara'a,Spark yace kune ashe,suka ce ae Yaya, Mufee ta mika Masa hannu wai su tafa,ya Kalli hannun yace sa'anki ne ni? tunda muke na taba handshake da ku? Kuna mata au kin manta uwar mu Daya uban mu daya dadina zaki ji Mufee? Baki suka bude da sauri Mufee tace sorry wlh gani nayi muharramina nane Kai,Spark ya kalle ta yace uhmm to ki fito da miji a muku aure sai kuyi ta handshake shine karshen kusanci Bada ni ba wannan iskancin na koma Dan kauye dankwali ya ja zakara matata ta Jani duk wannan iskancin bada ni ba,dariya suka yi Haly tace kawai dai fada kayi Yaya ba wani Dan kauye Itama ai ba Yar kauye ce ba,au na zaci ai zaku ce itama tayi clean yanzu kuci ubanku yanzu,suka ce a'a, Alright ya furta ku zauna. Naila ce ta fito da dan gudu da wayar tana taka steps tana kawo Masa tana yiwa su Haly barka da zuwa,Da wayar da hannun ya hada ya rike tare da jawo Naila ta zauna a tsakiyar cinyoyinsa,su Haly ya saci kallo yaga sunyi sauri sunyi kasa da Kai,yace dama Mima ta haifi masu kunya? film suka koma kallo ta dole,Naila tace akwai komai fa a kitchen kuje ku zuba kuci abinda kuke so,Mufee tace a kawo mana mudai kar ace munyi shishigi,to baza ta tashi ba sai dai in baza kuci ba ku barshi" ku baki ne ko gidan bakon ku ne,Haly ta mike Mufee ma ta mike suka nufi kitchen,Bayanta ta kwantar a kirjinsa Yana shafa gashinta yana danna waya,Spark yace gobe ranar ziyara ki shirya muje wajen Mero,Naila fuska ta bata Nan take,kishi ya cika mata zuciya,Jin shurun yayi yawa ya leka fuskarta yace Allah ya shiryeki Naila,tace Ameen zanje ai Allah ya kaimu. Fitowa suka yi da plate da lemuka Naila tace Kun min ta'adi fa amma ai duk daya tunda jininsa ne ku amma plates din bana kowa bane duk kalolin nasa baku ga na musamman bane,Haly tayi murmushi tace to ayi hakuri amma miji ma komai nasa ba a tabawa? Naila tace Kai Baku sani ba? to spoon ma kala kala sunfi kala goma duk irin nasa daban ne wlh Kuma kullum da kalar da za bashi ya ci da shi,plates ma haka nasa irin iri ne Kuma kullum da kalar da za a bashi komai da kuka sani nasa ba a tabawa na daban ne,Kai Sallaya ma sai da izininsa wani zai hau Masa,Haly tace ai Kinga mun karu shi yasa kitchen din kamar ana siyar da kaya,Naila tace ba a wasa,Spark Yana jinsu Yana danna waya har wani dadi yake ji shi Kam ana girmama shi ya Dade Yana mamaki ko cokulansa gasu da yawa iri iri amma baza a bawa wani irin nasa ba,yace bala'i da masifa ya kare akan Wanda baiyi dacen mace ba. Su Haly a gidan suka kwana abinsu sai abinda suka ga dama suke yi indai baza su taba mata kayan Spark ba to suyi komai ma,sun sake sun samu waje sai suka fasa tafiya suka yi zamansu a gidan, a gidan Naila da Spark suka barsu suka tafi Kano wajen Mero. Naila burinta taje taga su Goje ko zasu ganeta. Har da cewa amma zamu fara ganin Maza Wanda muka dan sani a Dan musu alheri ko ka samu Lada kaji please,Spark ya kalleta a jirgi yace kice kawai kina son ganin samarinki,Naila ta wayance tace daga nace kayi sadaka Dan Allah,banza ya mata yace kin ma rainani Ina kallo zan barki ki wani gaisa da kartan banza wlh idan kika kula wani a ciki ranki sai ya baci ya hade rai,Naila tayi shuru Yana ta faman tsaki har suka sauka. Haidar ne ya samu Jauro a gidan Amaryarsa Jauro Yana Palo Yana hutawa,Haidar ya shiga gidan,bayan sun gaisa ya gaida Maman Annoor ma yace Kawu dama fada Maka zanyi gobe zan koma gidana na zauna a can,Jauro yace aure kayi? Aure Kuma Kawu zanyi baka sani ba,to baza ka koma ba kana gida dadin kaje kana baligi ba kowa Kai kadai a gida ka dinga kawo yaran banza to ban amince,in kana so ka koma ka Nemo matar aure dama ka isheni,dariya Haidar yayi yace Inshaallah zan kawo matar auren Allah kawo ta gari, Jauro yace Ameen ko Kai fa kaima ai ko Dan Hubby ka samu me fada Maka amma kullum Haidar Haidar ba canji ko Hashimu ai an canja Masa suna shi da yake local ma ana fada Masa Abban Mohsin,mu kuwa da ba Da ba jika kamar samari muke ai mu sai Hubby,Honey,Sugar,Haidar ya dinga dariya yace Kawu yanzu in aka kiraka da Hubby sai ka amsa? Kawu ya furta na dade da amsawa ma tuni,yaro sa wasa ana ta ci gaba Banda kai gaka kyakyawa sankacece sai bulayi kake yi a gari,Kunkumar ma taki samuwa,Haidar dai ya Dade Jauro yana ta babatu akan ya samo mata shima,sai da ya gama fadan sannan ya Kalli matarsa Amarya yace a karrama min Dana da kayan motsa baki,dariya suka yi taje ta kawowa Haidar kayan ci da Sha sosai. Naila kuwa suna zuwa lokacin Maza ne duk,driver da ya kaisu yayi parking suka fito,Spark yace kinji me nace ai karki kula wani ko da wasa muje ya rike hannunta suka shiga,sai kallonsu ake yi kowa ya gane Spark Naila sai kallonta akeyi duk mazan Nan kallon sani suke mata sun rasa Ina suka Santa,Naila kamar tayi kuka tana kallon su Malam Jilani duk gasu Nan anzo musu amma Spark yace in ta sake tayi magana tam,su Goje suna ganin Spark da mace suka tabbatar Jamilu ce ba karya tunda shi ya aureta Kuma gata sun zo tare ma kowa ya kalleta yasan itace sai dai ta Kara kyau,ta Kara haske da kiba ta goge gata Kuma a shigar mata ta alfarma domin shadda ce a jikinta peach color. Masu Sharhi Ina godiya matuka. AsmaBaffa [2/14, 8:52 PM] AsmaBaffa: 🏫TANTIRIYA🏫 A GIDAN YARI BOOK 3 ~TAIMAKO~ 6-10 Official By AsmaBaffa SADAUKARWA NE GA AIDA MAMAN TASNIM PAGE NAKI NE Mariamsanee50 *ZINARIYAR MACE⚡* *Wai shin 'yar'uwa menene matsalarki? zubewar nono, ko kuma rashin kwankwason juyawa a falo maigida ya shiririce ya manta da tibi da matan tictok, menene matsalarki ne? rashin ni'ima ko kuma mugun sanyin da ya yi miki katutu, shin rashin taushin fata ne ko kuma kuraje da tabbani, ko bala'in ramar da ta addabeki kuma babu rashin ci ba rashin sha a gidan auranki, gwaigwayewar gashi ce matsalarki ko kuma kaushi da faso na tafin kafa da bushewar fata, kina bukatar fatarki ta yi glowing kalarki ta fita kuraje su mutu, ko kuma kina bukatar azababbun turaruka da humra tare da turarukan wuta. Na san dai kuna da yawa matan da tumbi ya yi musu karan tsaye ina nufin ya katse muku hanzarin yi wa maigida gwalli da muskuce-muskuce a falo😃 Nesa fa ta zo kusa AL-KUTUBIYYA ISLAMIC MEDICINE sun tanadar muku da nau'in magungunan da suke magance kowace irin matsala da izinin Allah. Babban burinmu shine sha'ani na aure ya inganta a samu daidaito. Muna da.* Na gyaran nono. Na sanyi. Dilka tare da hadin sabulu. Duk Wani nau'in maganin mata. Humra turarukan wuta perfumes, original miski tahra 3in1, ciccibi budurwar kaza. Had'addun supplement irin wad'anda ba su da matsala. Maganin Sliming wato narka tumbi. Abubuwan da muke sayarwa suna da yawa, kuma babu asarar dukiya. Muna garin kano kuma muna tura kayanmu kowane gari fad'in Najeria da Nijar har ma da kasashemn ketare. Kai tsaye a tuntu'bemu ta lambobin wayarmu domin karin bayani. *08089965176* *07084653262* Dan Indo Yana zaune wajen abokinsa kasurgumin Dan iska ne ya hango Naila ya saki salati sai da abokin ya Kalli Dan Indo yace lafiya? Dan Indo Naila kawai yake kallo yace wayyo Jamila wannan tafi karfin Jamilu sai dai Jamila, mikewa yayi Yana kallon Naila ya taka suna tafiya ya Sha gabansu,ko Spark bai kula ba yace subhannallahi kayyasa Chau Allah dai ya biya,Innalillahi wa innailayhirrajun,walahaula Wala kuwwata haka kike da kafirin kyau ban sani ba Ina Nan mun zama kartan banza,Naila tayi mukus ita tsoro ma abin ya bata,Spark fuska ya tamke ya Maida Naila bayansa sai ga Goje ta baya yace Dahara....Spark yace wannan wanne shirme ne? are you out of mind? Kun San wace kuwa she is my wife,Dan Indo yace and so? Ina ruwanmu da aurenta mu Jamilu Terror muka sani a bamu abinmu muyi ciki,dama Ina nemanka Dan wulakanci shine kaje ka aure ta uban waye ya saka ka aureta? Spark yace ubanka ne yasa ni stupid,Kai in ba jahili ba matar wani zaka kula,Ya ja tsaki ya fisgi hannun Naila yace muje,Dan Indo ya tare hanya yace wlh ba Inda zaku je sai ka bamu abar mu,Naila tace zanyi magana Dan Allah please hannunta ya matse da karfi ta saki ihu sai da ya ja hankalin Mutane,Scola ne ya tashi Yana taku da sauri Yana karairaya yace wayyo kawata Yar uwata haka madarar Nido ta Maida ke wata fresh and Beauty,gaskiya ne ai kin samu ta me kudi wlh abinki Shar yo Yar Nan kullum kaji da kayan marmari ba dole a fitar da Madara me inganci ba ,Spark yana Jan Naila,laaa Tantiriya ga Tantiriya,Shege Jamilu Terror Kaine haka? washer ya tafi da gudu Yana Jamcy Jamcy kamar zasu cinye Naila haka suke yi,Malam Garzali daga nesa yace Allah ya sanya Alkhairi amma kin dauki hakkin mu,ragowar bujenki suna Nan muna kallo sun zama kayan tarihi, Spark samawa kansa lafiya yayi ya Maida Naila bakin gate ya sata a mota ya shiga shima ya rufe,yace wannan ai sai su cinye ki duk ga mata nan ke kadai ce mace,Naila tayi shuru yace da ke nake fa,tayi shuru,yace wlh sai na sa an Kai Dan Indo dakin duhu an gana Masa azaba,Yana ta faman masifa Naila tayi shuru yace bana son raini,tace Kai fa kace nayi shuru kar na sake nayi magana sabo da haka nayi shuru. Dan Indo sai ashar yake durawa a filin ana rirrike shi,Yana cewa Dan wulakanci da cin hanci yarinya Bata gama wa'adinta ba ta gudu Kuma gashi tazo ana kallo ma'aikata suna kallo,Kuna kallo baza ku kamata ku dawo da ita ciki ba,sai na tona asiri yau nine Nan na fitar da ita ni na sa ta gudu,sabo da ta auri me kudi Yana Baku cin hanci shine aka kyaleta,ai nine na gayyato yarana yan Daba suka bude wuta a bakin gate da su Goje ta ciki muka samu bulalai muka Zane kowa,muka hargitsa kowa ta fice a sanadinta mutane da yawa sun gudu yau na fada kowa yaji nine.... Nan take securities suka kama Dan Indo suka ce zaka yi bayani,aka yi ciki da shi,Goje yace tab Dan Indo ya kira ruwa zai ci ubansa a gidan yari sai sun kusa kashe shi,Scola yace Allah na gode maka da ka sa min basira na koma mace. Spark kuwa Kallon Naila yayi ya ja Kwafa,sai da aka gama da Maza kaf suka koma sannan aka fito da mata,Spark ya kira Mero ta fito sannan suka karasa,Naila fuska a hade tana kishi da kyar tayi kokari ta danne,suka gaisa da Mero,Mero tace Naila Ashe kin San su Azima, Naila tace la na sansu amma a sanadin su Chika, ni Maza na sani a cikinsu na zauna a can muka hadu da my love ta furta,Mero tace kinyi dace Nima nayi dace,Naila tace ban gane ba,Mero tace to Nima Ina da nawa a prison,sai lokacin Naila taji dadi tace Allah yasa da shi za ayi kema in kinyi aure karki sake a Miki kishiya Kinga dai ni kiyi koyi Dani,Spark Yana jinta wai Mero take gayawa irin ta San mijinta ba aure zai Kara ba,duk ya gane hirar ta,a ransa yace Ina ma Ina da ra'ayin aure da na bawa Naila mamaki,Mero tana ji tasan ma da ita Naila take,ta mikawa Spark muficin da take sakawa tace gashi na iya? Spark ya karba yace sunyi kyau mashaallah na gode,tace nice da godiya,naso ace yau Innata zasu zo da ka gansu amma sun fasa wai sai gaba,kaga a ciki Ina zuwa makaranta na iya karatun Hausa yanzu na fara iya na turanci,ga addini,Kai na fara zama Malama yo duk su wankan haila,wankan janaba,wankan juma'a,Idi duk na iya ai inaga Nima watarana sai na bude makarantar koyarwa,Spark yace naga alama kinyi kokari sai ki dage Dan kin kusa fita an kusa fara shariarku,Naila kishi ya hanata sakewa taje ta kawo kayan da suka kawowa Mero harda abinci take away lafiyayye,ta mika mata tace mu tafi Spark na gaji kasan ba wata cikakkiyar lafiya gare ni ba,ta kankame hannun Spark mu tafi Dan Allah,ni mu tafi,muje gida kaina ciwo,tana Jan hannunsa,haka suka yiwa Mero sallama suka tafi ya shiga mota driver ya tuka su zuwa airport. Yanzu muficin Nan ne ya dameta a ranta da Mero ta bayar" Spark yasan baza ta kyale muficin ba" ya bata a hannunta sabo da ya huta da kishin Naila,suna zuwa gidan ta wuce da muficin bedroom dinta,kasan bed ta wulla su kawai tace shegu baza ayi fifitar ba,muna da Ac,ai tunda hannun wata ne ya saka ba me amfani da Kai har duniya ta nade, muficin ma ko kyau,in banda Maita ma irin ta sarakai mene abin so a nan,naga dai Spark ko me unguwa basu gada ba a danginsu bare ace, tsaki ta ja ta shiga safgarta. Washe gari Spark yace Ina muficin nan mu gansu na Mero,Naila tace naga dai ko me unguwa baku gado ba wlh ba me amfani da shi a gidan nan,na Kone shi ato kaji ka sani,dariya yayi a ransa yace ki dakko min abina,Naila tace wlh akan muficin Nan in banyi yaji ba Allah ya tsine min,sai nayi yaji na tafi gidan ubana,na gaji da ci min fuska da kake yi Ina Maka Kara da alkunya baka gani,mene bani da shi Wanda Mero ta fini,harda hawaye da kuka,Spark ya bude baki yace wai ke tsakani da Allah kishin Mero kike? Ni wlh ko sunanta ka kira gaba faduwa yake bana son zancenta bana kauna ka daina min ahhhhh....har da kururuwa kamar ta zare,Spark yace,to na daina ke Naila haka kike da kishi,yanzu idan nace aure zanyi fa,baza kayi ba...baza kayi ba Inshaallah daga ni sai Kai mutu ka raba takalmin kaza daga nan har tsufa, dariya ta bawa Spark,tace ba abin dariya bane ba a dariya a sharing din Hallare wannan ba abin dariya bane,ni bana wasa da harkar kishi,ta fututtuke sai kyaleta yayi. Yana Office Yana so ayi aiki ya tsare Rafeeq ya zauna a Office din ya sashi gaba,Rafeeq yace Abu ba Kara ba mutunci,Spark bai kulashi ba Yana ta danna wayarsa,Ikhram ce take ta faman kira,Rafeeq ya Kai hannu zai dauka Spark ya rigashi yace yi aikinka zan kular ma da ita,ai wlh gwara ka koreni na koma wajen Misam na gaji da wannan takura,ace waya ma bazan yi ba,Spark wayar ya daga yace aiki yake fa madam,Ikhram taji Muryar Spark tace a ranta Allah ya so ni banyi subutar baki ba shi yasa ba a so daga daga waya baza ka tsaya Kaji mutum bane sai ka fara sakin zance. Gaisawa suka yi Yace Yana jinki Rafeeq din,bana ji bazan yi magana ba idan baza a bani waya ba to Yana danna system Yana magana,Dan Allah kayi aikin Nan ba a tura ba har yanzu sabo da su na shugo Office banyi niyyar fita ba,ni wlh gwara ka koma wajen Misam din ma na kawo Arham ko Shaheed better sai kace yaro da matarka da komai aiki sai an tsaya a kanka haba Rafeeq,Rafeeq yace wai ba gashi Ina yi ba,to ci gaba yau sai yamma ba hutu,sai gaf da break Ikhram ta aiko da abincin basket guda,Spark yace Inye kaga masu mata,Rafeeq yace Kai muga naka,ai kasan ana kawowa nine nace kar a kawo yau kaga ma bata Dade da yin bari ba hutawa take,to ga Abinci nan in kana ci,Spark yace ai ni duk Inda naje yanzu bana iya cin abinci da yawa sai dai kadan maganin yunwa In na koma gida banci nata ba akwai matsala hanyar lafiya a bita da shekara,Rafeeq ya dinga dariya yace tsoro kawai kake ji Yaya,Spark yace banyi kuri ba ai ta cancanta a ji tsoronta,Rafeeq ya zuba abincinsa Yana cewa Yaya Anya kuwa Ikhram ba ciki ne da ita ba,Spark yace tooooo...yanzu aka ce har ta samu ciki da na bani sabo da Allah Ina wani amarci da na ci. Spark yace duk watannin da ka kwashe,Anfi 4mnths Ina laifi ai ka dangwali arziki,Dan tayi ciki mene a ciki ai sai tafi dadi ma kana hauka,Rafeeq yace Kai inaga ciki ne da ita Allah Kare ni bana so yanzu,baka so kaje kana kwanciya da ita, Rafeeq yace to gani ga Allah amma yau bata son kamshin kaza gobe Yalo zata ci,jibi tace wancen abincin ma ta daina ci ko ta dafa sai irin wannan ciye ciyen,ga masifar son sex,yanzu yau hakkinta ka dauka ka rikeni a Office ,Spark yace ta Nan ka bullo uban wa zaka yiwa wayo,tayi ta cikinta ba ruwana,Rafeeq yaji dukul a ransa yaso yaci nasara ya gaji,yace ka taimaka min Yaya Dan Allah,wlh ba Inda zaka sai 5pm ka gama aikinka. Basu tashi ba sai 5pm sannan ya kyale Rafeeq,basket dinsa ya dauka ya nufi gida abinsa Yana shiga Ikhram ta tarbe shi ta rungume shi yace yau Spark ya kusa halakani yau mine,fuskarsa ta shafa tace kayi hakuri ai nema ne muje kayi wanka ka huta, daukanta yayi suka shiga bedroom,wankan ma itace ta tayashi ya gama shiryawa cikin jallabiya ruwan Zuma,tace abinci fa? Yace na koshi sai anjima ya haura Saman bed ya kwanta Yana hutawa Ikhram ta hau yi Masa tausa daga tausa ya fara bacci tace nifa ba bacci nace kayi ba,I think i need you,Rafeeq ya bude Ido a hankali yace Anya ba ciki ne da ke ba kuwa wifey, yau ya kika yi da bana nan? Ikhram tace na Sha wahala sai addua nayi,Dan Allah ka tashi muyi,Rafeeq ya zaro ido yace da kin bari nayi bacci na tashi zanfi samun nutsuwa,Ikhram tace to yi baccin zan jira,ya koma ya fara baccinsa ta tasa shi gaba kamar mayya tana ta kallonsa tana kallon agogo. Minti talatin tana cika ta fara murna tace lokaci ya ja,tana zaune a tsakiyar gadon a gefensa tana kallonsa kwanciya tayi ta shige jikinsa tana ta Allah Allah ya tashi itama tayi baccin,har magriba ya rigata tashi ma,ya tashe ta yace lokacin Sallah yayi ya wuce masallaci,bayan ya dawo abinci ta shirya musu suka ci suka koshi sannan suka fara Kwalbewa abinsu,Ikhram yanzu bata gajiya,jinta yake kamar sabuwa ta Kara sweet shi yasa kullum sai Kara nacin masifa,ko bata nema ba sai ya kunnata bare ma kullum a cikin bukata take. Washe gari sabo da Spark yaki kunna wayarsa bai fita ba,Spark har gida yazo daukan Rafeeq yana mota driver na tuka shi,yasa me gadi yaje yace Rafeeq ya fito,Rafeeq daga wanka ya fito ya shirya a gurguje ya fita Yana cewa a kawo Masa breakfast Office,mota ya bude ya shiga Yana fushi,Driver ya ja suka tafi. Abba kwance yake a katifarsa ta shago Yana Jin radio,Kubra ta leko tace kaji kunya wlh ko ni mace bazan yi wannan lalacin ba,Abba yace na zaci ma zuwa kika yi ki tayani kwanciya nafi Jin dadin auna hatsi,bazan zauna a benchi ba ga zafin rana so kike cutar rana ta kamani na dinga kashin majina wlh bazan yi ba,bazan zauna a rana ba sai Rumfar kwano me shegen zafi,ke yanzu ba ci gaba bane a Ganni a killace a cikin shago amma a rumfa kowa Yana kallona tsirara iska tana bushe ni da rana,idan ana ruwan sama Yana min feshi,Nan kuwa a cikin sutura,Yar Inna ko dai kin daina so na nane ban sani ba? in kin daina kaunata ki Fadi gaskiya sai na Kara aure babu Bata lokaci,naga kwana biyu wani gani gani kike min,Kubra tace me yayi zafi daga magana daya,yace to kija baki kiyi shuru, dubu biyu nazo karba,Abba yace to ana sana'a Kuna korafi sai Kuma a baku-a baku gashi ya mika mata" ciki ta shiga ta samu buhun Masara ta zauna Abba yace ahhhh....ta mike da sauri Dan taji tsoro ma yanda yayi yace abincin ci ne fa ki zuba Masa wannan mazaunai ai ba tsari tashi gaskiya in baza ki zauna a katifa ba ki tafi gida,Kubra tace bazan tashi ba wlh na zauna,Dan Allah ki dawo Nan Kinga Sha wuya ya nuna mata katifar da yake zaune,tace bazan dawo ba a nan zan zauna. Abba ya kalleta harda harde kafa yace to ya soyayya ta Yaya tunanina ? Dariya Yar Inna tayi ba shiri ka fa girma ka daina irin wannan ka barwa su Mohsin,Abba yace sabo da sune mutane ni ba mutum bane soyayya ba tsoho ba yaro kowa ya ji da tasa ai bakya kunyar ciki sai soyayya,in ciki ne yanzu zaki ta amai a gaban mutane ki ta asarar abinci kici ki amai,Bai fa kamata na yafe miki ba da aure na kike tafiya wajen gardawa amma na yafe miki Dan Kinga nayi shuru da zancen Ina sane,dariya Kubra tayi tace rana tana yi bari na tafi girki zanyi,Abba yace ke rabu da girkin nan yau a siyo abincin, mu nawa ne kwata kwata a gidan zauna muyi soyayyar mu,Yar Inna tace dama na gaji wlh,Abin nema ya samu Abba yace ba shegen da zan siyarwa ko da gero ne bazan siyar ba yau tunda kika kawo min ziyara,Kubra tace a gida fa muke wannen shagon a Jikin gidanka yake Ina wata ziyara a nan,Abba yace duk da haka idan ba haka ba duk Wanda ya siyi kwano Daya biyu zan bashi,Kubra tace a'a ai gwara karka siyar ni tafiya zanyi,yace kina tafiya zan rufe na dawo gida. Jauro ne ya kira Abba,ya daga yace hello" kana magana da Hubby,Abba yace waye Hubby? Hubbyn ubanwa kamar wani Dan Daudu ni bana Daudu Allah ya tsare ni,Jauro yace Kai dalla daraja na Kara na samu Karin suna,ai duk suna Daya in ka samu Kari to darajarka ta karu,Amaryata ce take fada min,Abba yayi dariya yace to sai aka yi me? Kai dadi kake ji nufinka? Karya take" fada tayi Dan kaji dadi wannan lokacin soyayyar an wuce lokacin ka gama abarka da Habiba tun da jajayen sawunka,itama ta gama soyayyarta da me Yalo uban Annoor ka daina murna Jauro,ni kaga nawa kowa yaji yasan ba karya a ciki Abban Mohsin Kuma ni na haifi abina akwai wani shege da ba ni ba,Abban Naila, mutane suce mijin Kubra,Yar Inna in soyayya ta Kai mata tace Dan siriri na kaga duk ba karya siririn ne ni,Kai kuwa wlh ka kiyayi Hubbyn nan da gemunka da furfura a dinga fada Maka Hubby ko dacewa baka yi da Sunan ba,ai gwara me gida ma ya fiye Maka. Jauro yace bakin ciki kake min Hashimu na gano ka,ni ban San ma wanne kuskure ne yasa kazo a abokina ba,gaba daya abota da Kai kaddara ce ma,Hashimu yace to ya zaka yi Dani baka da kowa sai ni sai na zo cin girkin Amarya,Jauro yace Dan Allah kazo kaji dadi,Kai kaga wani Yankan salat me sifirin kamar ba hannu ne yayi ba yir yir yir indai yanka kayan lambu ne a barwa Ruhina,Abba yace ita Kuma Habiba fa mece? Jauro yace ita zuciyata ce Amarya Kuma Ruhina an barka a baya ka zauna da mace daya tilo kullum Kubra Yar Inna wai Dan Allah baka gajiya? Abba yace ka ganta tana jinka tana shagona zance tazo ma yau nace ta huta mu soye bana gajiya da abata ko? Abba ya Kalli Yar Inna,murmushi tayi tace Jauro ta Allah ba taka ba inshaallah baza a min kishiya ba,in naga dama sai na raba abotar taku,Abba yace wannan Kuma kinyi karya karki mike kafa dai ba a bawa namiji Amana Nima ba wata Amana zan rike ba ko yaushe zaki iya Jin kishiya ta taho" karki yarda dani bani da tabbas,Kubra dai tana jinsu suna ta surutu. Misam ne ya Kai Chika asibiti daga Nan ya kaita gidansu,Kamal suka samu da Spark a kofar gida suna ta hira da tsare tsaren bikin Kamal da za ayi Nan da sati daya,Misam ya budewa Chika mota ta fito ko kula su baiyi ba ya sa Kai zai wuce,Kamal yace Amma baka da mutunci yaron nan,Misam yace to Kunga real namiji sai na tsaya Ina kula ku Kai baka da mata a kwararo kake kawai,shi Kuma wannan yayi auren Dan cikin ma ya kasa ba rashin kunyar da basu yi ba an kawo Amarya amma ni zuwa daya kawai har ta karba,Dariya Kamal yayi Chika ta gaishe su, Spark yace masu ciki gashi Nan duk kin dashe mu kuwa dama karkar muke ko da shi ba a ganewa,Misam yace wlh a'a kasan dama ba Wanda ya isa ya kirata da baka ato,matar taka fin ta wani tayi,Spark yace Allah ya baka hakuri masu Hallare da Madara,Chika tuni ta wuce ciki tana dariya, Misam yace Ina Rafeeq? Yana Office na bashi aiki yanzu ma wajensa zan koma nasan halinsa yanzu sai ya tafi gida. Annoor yau Iman taci sa'a ya kyaleta ta kwana lafiya,suna zaune Jauro ya kira Annoor yace Ko me kuke ku bari muje asibitin mahaukata Maman Iman ance ta dawo hankalinta,Annoor yace to bai fadawa Iman ba sai yace ta shirya suje gidan mahaukata su gano mamanta,sai murna take yi ta shirya,Annoor bayan ya shirya ya saka Shadda wata sky ya zuba kyau harda dora Yar hula a Saman kitsonsa yace zanje wajen surukata tunda ta warke ai taga surukinta kamili,Kansa ya kalla a mudubi ya juyo ya Kalli Iman yace ya kika ganni? tace Kamilu Sunan wani,dariya yayi yace tambaya nake nayi kyau please? tace to Kai akwai ranar da baka kyau ma ai kullum kyau kake yi,mudubi ya sake lekawa yace wow Allah yayi kira,dariya tayi ta ture shi tace kalle ni fa,me zan saka ne ma na sutura? Yace Abaya,ai kuwa ita ta zabo wata maroon Egyptian ta saka tayi kyau sosai kamar a sace ta. Suna kamshi suka fita shi ke driving a wata sabuwar motarsa da ya siyo,Kawu suka dauka suka tafi can. Suna zuwa aka kaisu wani daki na daban,sannan a kirata ta fito sanye cikin riga da zani na atamfa har da Hijab,kana ganinta kasan yanzu da hankalinta,shuru tayi tana kallon su,Nurse tace gata Hajiya ki musu magana su suke zuwa dubaki,Jauro yace sannu tace yawwa Dan Allah ku su waye ku kaini gidanmu,Iman farin ciki ya kamata,Maman Iman tace ni Yar kauyen Libiya ce tallan maganin gargajiya ne ya kawo mu kasar Nan da iyayena,Jauro yace zauna Dan Allah ki nutsu ki bamu labarin naki ko zamu San Inda zamu kaiki. Zama suka yi sannan tace sunana Rahma,Jauro yace yawwa ko kefa Rahma suna me asali,taci gaba Babana sunansa Mahmood tun Ina karama ya rasu,Mahaifiya ta ma Ina karama ta rasu a wajen kakata na girma wacce a kauye muke da zama,tana bada maganin gargajiya,tana amfani da Aljanu,kasa kasa muke zuwa,watarana muka sauka a Nigeria a Daji muke zama da dabbobin mu shanu da rakuma,akwai wani bawan Allah Dan asalin Sudan ne zai wuce Abuja ya ganmu a hanya ya tsaya ya karbi maganin haihuwa a wajen kakata,ta bashi yace Yana so na sai tace baza ta bashi ni ba ya nace a haka dai sai da yasan inda muke zaune a Daji. Watarana yazo wajena ya samu Kakata bata Nan ya bani wani abinci me dadi da nama tunda na ci ban sake sanin Ina nake ba Ashe magani ya bani yayi amfani dani ya lalata min rayuwa,Sai da kaka ta dawo ta sameni cikin wani hali na fada mata komai amma sabo da taurin Kai Ina sonsa yana so na tace baza ta bashi ni ba,ni Kuma nace tunda Hakan ta faru ai gwara kawai ya aureni a huta,shi Kuma dan Sudan Marwan kenan yayi min haka ne Dan Kaka ta bashi ni ya aureni amma taki yarda. Ana nan watarana na dinga kuka nace wlh sai na bishi mun gudu,tace indai na sake na bishi sai ta Sa Aljanu sun haukata ni,ban yarda ba watarana muka hada baki da shi muka gudu ya dauke ni a mota,kwana daya tsakani na fara ciwon hauka ban San Inda kaina yake ba,da kansa ya dawo dani wajenta,ranar da ya kawo ni ranar Kuma ta bawa wasu Yan fashi magani sun gwada bai musu ba suka dawo a ranar a gabana suka yiwa kaka Yankan rago suka fece,har a lokacin bana gane abubuwa da dama hankalina ya fara barin jikina,daga nan nidai ban sake sanin Inda nake ba sai yanzu da Allah yasa na warke jiya kenan. Jauro yace iKon Allah to ko dai Marwan din Dan Sudan shine uban yarki? Tace wa? Ya nuna mata Iman ya kwashe labarin komai ya fada mata,Rahma tace ya kamanninsa suke? Jauro yace Yana da haske dogo yana da gashin Baki goshinsa da tabo,Rahma tace wlh shine masoyina nane Ina sonsa har yanzu a Abuja yake zaune cikin gari yanzu Ina zan ganshi. Jauro yace Yan uwanki fa? tace bari tukun wannan duk suna Libiya Kuma ma duk sun tarwatse bada magani yanzu burina a Nemo min Baban wannan da kuka ce Yata ce,yanzu wannan 'Yata ce?Jauro yace yarki ce gashi Nan Kuna kama ma,Iman sai murna take yi tace Kinga mijina surukinki ne wannan ta nuna mata Annoor, Annoor yace Ina Kwana harda kasa da Kai. A ranar aka gama komai aka sallami Rahma suka wuce gidan Habiba aka Kai mata ita ta zauna a nan,sai Iman ake tayawa Murna. Jauro yace Haidar ya shirya dama za aje wajen ubansa mahaifi a Abuja sai a tafi da Rahma ko za a ga uban Iman a can,Habiba tace ya kamata a bari ta murmure sai a je. Mahaifin Annoor ya dawo daga US ya samu Yarsa Maryam tana cuta ta gaske an rasa dalili ta rame ta fike,ga wasu kuraje da suka cika mata jiki kamar me Karzuwa ba kyan gani,komai sai anyi mata,haka mahaifiyarta ba maganin da bata karbo mata amma shuru,yace Maryam me ya same ki haka? Maryam tana kwance Saman bed tana kuka ta kwashe komai ta fada Masa,salati yayi yace ai gashi kinwa kanki,Dan uwanki ne shashasha,Allah ya Baki lafiya amma abinda ya sameki kin cancanta ya same ki,bani address din Annoor din,tana numfarfashi ta bashi tace ga wayata Nan a jaka akwai number dinsa ciki. Hanif zaune yake a dakinsa Yana Shan yogurt da Dan wani spoon na roba yaji dadinta yace Inama wannan Khadija din tana Nan a bata ta Sha taji,a fili yace to Ina ruwanka da ita wai,Mero ce tayi magana tace hello ta sake daukan Karfenta taci gaba da bulawa sosai yanzu ta Burma wajen yanda hannu zai iya shiga guda Daya tace Hakan ma ya isa. Hannunta me kyau ta mika tace Yaya Hanif Inama sunana Hanifa sai aka sa min Khadija,Babana da kyar ya yanka min ragon suna ance sai da nayi Shekara uku a duniya aka yanka min Kuma wai Yar tinkiya ce ma,shi yasa ma akace bani da kan gado sabo da tinkiya aka yanka min,Hanif ya kwashe da dariya yace wai ke Dan Allah mene birgewarki Dan kin fada,bakya gajiya da surutu a rayuwa,Mero tace ai gaskiya ce dole na fada,yanzu gashi Ina ta koyon yanda zan kame harshe na,tsohon skirt ma da muke tatar Koko da shi ai an Dade yanzu da dankwali na muke yi,ai an samu ci gaba,Kuma da wlh kwandon wanka da muke saka soso da sabulu daga bandaki ake dakko shi mu tace taliyar mu muci Kuma gani lafiya kalau ba ko malaria,Kuma mu bama banbance botikin wanka Dana aikin gida sai muyi wanka da baho mu fito da shi mu kwaba danwake a ciki mu zilillika abinmu. Hanif yace gaskiya ku kazamai ne,Mero tace ai na waye yanzu tunda aka kaini aikatau na gane komai,da naje ganin gida baka Gani ba yanda na dinga cin gyaran Innar mu,tasowa yayi yazo Inda ta fasa tace Miko bakinki kiji,Mero ta cuno Baki ta cikin kafa tace wlh bakina karami ne karka min kiss wallahi Allah ni bana son Kiss yanzu,ban shirya Shan yawu wani ba,ba a haifi Wanda zan Sha yawunsa ba ni ba Yar iska bace nidai,Hanif tsaki yaja yace ke me zanyi da bakinki baki da hankali,ko wacce zan aura kafin ta mutu ban taba mata kiss ba,Mero tace Alhmdllh Rabin wata ne,Khairat ba rabo ba tana murna tace gaskiya ka fado duk wayewarka ka bari ta koma ga Allah haka ko da yake ba rabo ba. Share ta yayi Yana jinta tana dariya Spoon din ya sa ya ebo yogurt din ya miko ta kafar Mero ta bude Baki ya zuba mata ta shanye harda zaro harshe tana cewa wash dadi...dariya yayi yaci gaba da bata tana ta sha a haka,Mero kasa kasa tace na sace zuciyarsa saura furta I love you,Azima ta duba ko Ina Bata ga Mero ba dakin ta duba ta samu Mero manne a Jikin bango ana Miko mata yogurt tana Sha tana Santi. Azima tace Mero me kike yi haka? Mero hannu ta daga ta baya tace ciyar dani ake yi,shi dai Hanif bai san me suke yi ba Azima tuni ta ture Mero ta mika nata bakin yaci gaba da antayawa Azima itama a baki,Mero tace Kai Hanif Kalli labbanta bakake bafa ni kake bawa ba Azima kake bawa haka labbanta suke bakake? Sai lokacin Hanif ya duba da sauri ya janye yogurt dinsa,ya hau masifa kin cuceni kin Bata min lokaci,Mero tace rashin fahimtarka ce amma ai ka dinga kula,Hannu Mika ciki tace ungo,Hanif ya kama yatsanta yaji Laushi,yace ke a haka Yar aiki ce? to gona nake zuwa me ka Mai dani so kake kaji kamar bayan kada,Hanif ya dan rike hannun Mero yace Bismillah zunubi a kanki,dariya tayi Azima tace Dan Allah kizo mu tafi. Hanif yace wai Ina ruwanki ne kiyi tafiyarki kin takura mata fa,Azima kike ko wa ki shiga hankalinki. Azima ta juya ta fice Hanif yace Khadija ya kirata a nutse,ta amsa Masa yace ki dinga zuwa kullum zan koya miki rayuwa naga baki Santa ba,ya zaka ce ban San rayuwa ba gashi Ina cikinta kace ban sani ba,Kaine ma zance baka San rayuwa ba tunda Kai kana da kudi rayuwar kudi ka sani,ni da muke talakawa mu muke cikin rayuwa,yace baki gane nufina ba,tace to zan dinga zuwa ai inshaallah. Bayan kwanaki Mero kullum sai taje sunyi hira sun hade hannu waje daya ta Yar kafa wai kawaye ne. Spark gajiya yayi yace wai Baby har yanzu Jinin Bai dauke bane wannan bari ko masifa,haba sabo da Allah sati biyu ai nayi tawakali,murmushi Naila tayi ya Dade da daukewa tace bai dauke ba tana ta faman gyara kanta,sai da taga ya damu ta tsokane shi tace bai dauke ba,Spark yace ya Ilahi in ba Dan iska kike so na zama ba ya dauke haka mana,ni ba a halicceni nayi hakuri da Bado ba,ba hakurinsa nazo duniya ba wlh in zai dauke ya dauke kawai,Dan Allah ni a bani haka,Naila Ido ta zaro, yace wlh na gaji ni na gaji,Naila tayi dariya tace ya dauke fa yau,dama dazu nake cewa zan fada Maka,Spark yace da Ina da hanci da nayi guda,Allah ya miki Albarka a bani kar ya dawo ko labewa yayi ban sani ba gwara nayi abina. Kaya ya shiga cirewa Naila yace a gidan ma sai an toshe ko Ina,Ina ta so nayi sabon ciki ba hali,sai kace yau aka kawo Masa Naila gidansa yanda ya wani susuce ya zauce. Naila tace ka nutsu please,Ina zan nutsu yanzu ni bani da nutsuwa,Naila tace haka kake baka da nutsuwa yace ae Ina naga wata nutsuwa ni dama ba nutsatse bane,ai idona idon Boobs ko bado to sunana mahaukaci lokacin,Naila tace amma iya nawa ko? Spark ya tsokaneta yace harda uhmm ..uhmm..harda...uhmm...Naila tace bana mood,dariya yayi yace ai kin sani kema ko munyi fada ba abinda zan canja,ki kalleni so na ya miki yawa,Naila tace Allah ya kiyaye,yace handsome Irina,komai haduwa,ga kyau ta ko Ina Hallaren ma me kyau ga iya Uhum,ga sarrafa uhumhum,ga umm...uhmm,dariya suka yi sosai,Naila tace shi yasa nake sonka wlh Dan Allah karka min kishiya Dan girman Allah Ina rokonka Dan Spark dina,Dan nishadin Nan bazan iya gani an raba shi ba. Arham ne ya shugo da mota Yana parking ya shiga ciki Yana fushi Mima ya samu da Papa a Palo suna hira ya shiga ciki yayi Sallama zai wuce,Papa yace zo nan,wajen Papa ya nufa yace me aka yi Maka ne? Yace kawai a waje ne,wai Papa wata kwaila ce daga ganina ta zageni,Papa ya zaro ido yace Kwaila? Arham yace to dai ta fara kudi kadan,kudi sun Dan fito mata,kawai ta zageni bafa cewa nayi Ina sonta ba ko kulata ma banyi ba wlh wai dalla Dan iska,Kuma tazo ta bangaje ni. Mima tayi dariya tace to ba sai ka rama ba,na Isa na rama kasa ramawa nayi ta min kwarjini Yar mitsil da ita Kuma Baku Gani ba wlh Kuma taci banza ko gobe na ganta bakina kanin kafata,Papa yayi dariya yace to ko da ita za ayi ne? Allah ya kiyaye wannan banda kunya me zata yi,Au baka son kunya kunya ai ado ce,a'a ni bana son me kunya nafi son tsagera,Papa yace Allah ya shiryeka Arham yace Ameen ni Papa in kaga tsagerar ma ka samo min,Papa yace ka bani zabi? Arham ya zaci wasa yake yace ae,shi kuwa Papa dadi yaji an bashi zabi yace karka damu sai ka yaba yace to ko wace zan so ta,kayi alkawari? Arham yace Inshaallah Yana dariya,Papa yace an gama jeka ya wuce. Masu sharhi Ina godiya AsmaBaffa [2/15, 9:48 PM] AsmaBaffa: 🏫TANTIRIYA🏫 A GIDAN YARI BOOK 3 ~TAIMAKO~ 11-15 Official By AsmaBaffa SADAUKARWA NE GA AIDA MAMAN TASNIM PAGE NAKU NE ~htanimusa'idu Hanifadliman Washe gari Spark makara yayi yau jam'i ma ba a samu ba sabo da Kwalbewa ta kai,Naila tana ta baccinta hankali kwance,yunwa ce ta tashe shi ya bude idonsa Naila ta Dora kanta a nasa tana ta bacci" ya ture ta Yana murmushi yace Ashe cikin bacci Ina ta cin wahala Ina nishi kin danne min Kai,har yanzu mutum bai iya kwanciya ba sai yaushe zai iya,Ina Jin jiki billahillazi kullum daga na farka naga kafa a kaina sai ciki a kaina, maganganun sa ne ya farkar da Naila ta bude idonta a hankali" baya ta juya Masa ta sake Jan bargo, yace a'a ai gwara ki juyo na Kalli muninki sosai,dariya tayi ba shiri tace Allah ya kiyaye,burinka dama sabo da sa Ido ka dinga tashi da wuri kana karewa mutane kallo,dole Kai sai kaga kuskure salon ka Kara aure wlh bazan yarda da wannan ba,tashi yayi yace yunwa nake ji ki tashi bacci ya kare, mun makara kusan karfe tara fa,wayarsa ya jawo ya latso number Rafeeq. Rafeeq Yana gani Yana daga kwance yace na shiga uku Kuma ya daga,ka shirya ka tafi meeting bari na tura ma address yau bazan je ba bana Jin dadi,Rafeeq yace to yanzu a duniya dama wa yake Jin dadi nima ba dadin nake ji ba,Spark yace ba irin wannan ba Mura nake yi,Rafeeq yace to ai zanje ba sai ka likawa kanka cuta ba,duk da hakan dai ba a fimu komai ba kullum manne da mata an kasa komai mu da ake takurawa gashi muna ta samun Karuwa,Dariya Spark yayi yace wato idan Allah bai baka Abu ba tun daga gida,danginka, naka na jikinka shi zai fara Maka gori ya ci Maka mutunci,dariya Rafeeq yayi yace Kai ka jiyo dai bari na kira yaron nan korarren Soja ya kaini,Arham wai ya gudu Shima? Da kansu sojoji suka Kore shi,karya yake ba guduwa yayi ba,ai sai da Papa ya Maida shi sannan suka fada Masa. Aiki aka kaisu gidan Oga zasu yi gadi ya samu 'Yar Ogan tazo wucewa wai tayi shigar banza yaje ya rungumeta ya taba mata nono,Shine ta fara masifa ya zaneta ya mata dukan tsiya,tun kafin a Kore shi ya gudo gida ba Wanda ya sani ya canja school ma salin alin,shine suka Kore shi sabo da Papa wlh suka kyale shi haka, da yaci ubansa wajen sojoji Dan kawai Yana da kafa ne suka kyale shi,sai da Papa yace sai ya koma aikin sojan shine da yaje suka fada Masa abinda yayi suka ce ko ya dawo bazan su karbe shi ba. Spark yayi dariya kamar ba gobe yace Allah ya kyauta wannan yaro Anya Mima ta kwalbe dai dai kuwa Yanda Al'ummar Annabi suke Kwalbewa anya kuwa sanda aka samu cikinsa Ina Jin sai da suka yi fada da Papa mala'iku suka mata tofi bana kwarai ba,Dariya suka sake yi Rafeeq yace ai Arham shi Nono bai Masa kwarjini ba abinda ya Sha kansa wannan abubuwa basa Masa kwarjini,rannan ya koma na Mima yake nema,Spark yace Kai wannan yaro kwai Dan iska Ina saura a nan Papa ya gama da shi,Khalil,Ni kaina,Misam,Anam,Badia sauran duk gasu nan,Rafeeq yace saka da ni I swear ko Papa yanzu bazai kalle su ba to me zai ci da su,Spark yace ba ruwana bazan yi gulmar iyayena ba na kasa Jin kamshin Aljanna,Naila ta kare mata nine zan daga ta shige Aljanna Kuma tuni na daga mata ni Kuma su Mima ne,Naila ita ta haye wlh so nake mu hadu a Aljanna muci gaba da Kwalbewa,shugabar Hurul ayni kenan,ba wata sai Naila ko a lahira da ana zabi zance Naila Only to tunda ba zabi dama itace Shugaba ince tayi ta mulki ba mutuwa shike nan Kai nifa ko a can bazan yi adalci ba,Rafeeq yace wlh da sake akwai dalilin wannan kalaman naka Naila an mata tsumi na musamman daga kauye kace zan kawo Ikhram,kasan kuwa ka zauce Spark da safen nan ka tashi kana wannan darsa kalamai ai da dalili,Naila tuni tana wanka bata san me suke yi ba. Spark yace mota zan siya mata yau ba sai gobe ba,Rafeeq yace nifa kasan dangin Miji ne wlh zan fito da halina na bakin cikin dangin Miji ni me yasa baza ka canja min ba sai ita,ta shiga uku da sharrin dangin Miji kuwa za taga tuggu,Kai komai matarka baza mu yarda ba,daga tashi da safe,Spark yayi dariya yace ashe baki ciki zai kashe ka,Ina laifi ma da nake baka huge amount of money as your salary,idan Misam ne wlh bazai biyaka haka ba uban me kake yi a Office din,sai yanzu ma da nace Uban me kake yi na tuna wani Dan Indo a prison ya zageni,wlh sai na sa an Saba Masa kamanni wai Uban waye yace naje na auri Naila,bai sanni bane,Rafeeq yace to tunda Yana prison ka rabu da shi mana ya karata da hukuncinsa,Spark yace wlh bazan yarda ba sai an Kara Masa akan na baya,sai yasan ya zageni,ni da matata in banda karfin hali yace uban waye sabo da yana gadara shi Hire killer ne,kwanana bai kare ba ya isa ya kashe ni. Dan Allah ka rabu da shi kar muzo muna zaune lafiya ka jawo mana irinsu wlh basu da Imani sai su turo har gida a kashe mutum,Spark ya furta bafaa zan hakura ba,Rafeeq yace ai shike nan Mima tace tana nemanka kaje,ae yau zanje dama,Naila ce ta fito a wanka ta canja riga da sauri ta tada Sallah,wayar ya kashe ya shiga wanka Shima,kafin ya fito ta shirya cikin wata Yar guntuwar gown iya gwiwa sama ta tsuke kasa ta bude me gajeren hannu,pink me adon flowers red tayi kyau. Yana fitowa shima Sallah yayi da addua sannan ya shirya cikin wani yard me kyau fari tas ba karamin kyau yayi ba yana kamshi ya fito kitchen ya sameta,ruwa ta zuba me dan dumi ta zuba Masa Zuma me kyau ta mika Masa ya shanye sabo da Karin lafiya kafin yaci komai,a kitchen ya zauna suna Hira tana soya dankali ya hada tea dinsa itama ya hada mata, a haka a kitchen din suka karya,yace shirya ki rakani gida,tace to ta wuce sama,yace karki Dade please,sai da ta wanke toilet ta gyara bedroom iya Inda itace take gyarawa sannan ta hau shiri" Abaya ta saka Arsh me tsada ta dakko jaka da takalminta,Me aiki ta gama gyara Inda ya dace ta fito tace Uwale ki min wanke wanke ki gyara kitchen please,tace to keys din bedroom dinsu ta zuba a jaka Wanda ta kulle ko Ina sannan suka fita,yace duk da haka kin Dade me kika yi? Sai da na gyara bedroom da toilet ya zan fita gidana da kazanta. Spark ya dafa kafadarta yace ban gane gidanki ba? ta Ina? dariya suka yi ya rike mata jakar har mota chewgum ya sa mata a baki guda Daya Shima Yana cin nasa,driver ne yake tuka su suna bayan mota abinsu,Naila tace Baby" ya amsa na'am Baby,wayarta me tsada iphone ta nuna Masa tace kaga wasu takalma latest a siya min ta nuna Masa,ya gama kalla yace sabo da ga me rijiyar kudi ko,har yaushe aka siya wasu har yanzu na lefe Baki gama saka wasu ba kika ce a siya miki wasu ban damu ba na siya miki yanzu wannan me za ayi da su,bazan siya ba sabo da samun waje Kinga mutane da yawa akwai Wanda suka kwana da yunwa wlh bazan siya ba gwara naje nayi sadaka da kudin,yanzu ma na ware wasu kudi a iya Yan uwa da abokan arziki sai sun kare a taimako, Naila ta Harare shi ta dauke Kai tace zaka zo ne,yace Inzo din"yana dariya,buga kudi nake yi,in ana aiki ba a baki Hallare ba kin dinga korafi kenan ke an daina sonki. Naila tace to tunda baza ka siya ba sai ka kyaleni Kuma ai,tace ga Data can in zaki ci a siya miki na Naira dari dai ya isheki ko dabino ma kin gani fresh one,Naila ta Masa banza yace Nidai bazan siya ba Kuma sai anyi fara'a dole ya girgiza mata kafada ba shiri tayi dariya,yace ko kefa wayarsa ya zaro ya nuna mata motoci masu kyau Yan 8m zuwa 10m,yace mota zan siya sabuwa zabar min,Naila baki ta tabe tace ai ku son kai ya muku yawa idan kanku ne yanzu za aji Kuna kashe kudi banda matan ku,yace naji nidai zabar min,ta nuna wata baka Yar 10m tace wannan tayi duk tafi birgeni,yace okay,Gidansu suka je suka samu Mima da Mummy suna kallo har yau Mummy taki komawa gidanta,Spark ya nufi wajen Mummy ya gaishe ta ya zauna kusa da ita,ya kalleta yace Uwa ta,tace na'am nice nan gani,Naila Mima ta gaisar sannan Mummy ta zauna tana cewa Ina su Arham? Mima tace suna nan zaki gansu yanzu kuwa. Spark Mima ya gaisar yace wai kina nema na? Mima tace dama gidan Badia nake so kuje Dan Allah ai dai Kwa dan Kai matan naku,na fadawa Misam da Rafeeq ma,Spark yace ba damuwa, da gidan Anam da Khalil,Spark yace ba matsala za muje Inshaallah. Arham ne ya shugo palon da cup a hannunsa sanye cikin 3qtr da Yar t-shirt dinsa ga uwar suma,Mufee ce ta fito da gudu tace wlh Mima kice Yaya Arham ya bani abina,Arham yace me? Mima tace kaga bata abinta komai mene,cup din ya mika mata yace gashi kina Sha yau sai kin kwana kina zawo munafuka. Spark ya mikawa Hannu yace Ina me dakin taka,ya juyo ya Kalli Naila yace Me daki,Naila tace kayi kudi ka guje mu,yace zanzo ne ai kwana zanyi,Spark yace a Ina? Kana da gidan Uba wai ni na haife ku ne? Kun takura min fa,Arham yace wlh sai na zo tunda kayi gida da dakuna ai da baka son mutane sai kayi 2room and parlo,in Kun gaji dani ayi min aure,babu me sake aure a gidan nan sai Nan da 4yrs mun gaji,Arham yace za kuwa kuji bikina kwana nan,Mummy tace wannan Kai banda sakin aure me zaka iya,wa zai Maka aure yanzu me ka sani a duniyar 26yrs in banda ma kayi saurin girma yaushe amma gaka Nan Kai da Rafeeq kanku daya,Shima Shaheed din haka,Arham yace abin ne ya matso ya za ayi dani,Junior ne kawai ba ruwansa,Me balagar zuci cewar Arham ai ya Dade da balaga a zuciyarsa,Spark yace Arham zo na aikeka,Ni bani da zuwa a karami ba kowa ya taso da aikensa sai dai yace Arham,an haifo ni a karami Mima me yasa ba ayi kwazo ba a kaina,Mima ta mike tace Kai ni wai sa'arka ce,wai ni wannan yaro kuwa shine kuwa a mahaifata sanda Ina da ciki ba canji aka min ba,Mummy tayi dariya tace ato in kin San babu addua aka yi dai kiyi magana tun wuri,Mima ce ta harari Mummy tace Allah ya sawwake miki a gaban danki,Spark yace a'a'a'a tayi maganarta me za a boye min nasan white and black,Naila tuni ita tabi Arham sun tafi wajen Papa. Suna zuwa a bedroom suka same shi,Arham yace Papa gata na kawo Maka samfur ka gani irinta zaka samo min,Papa baiyi niyyar dariya ba sai da ya Dara yace to Arham ni da aka bani zabi sai an kawo min samfur,gwara da samfur ku yanzu idonku yayi dishi dishi kar a dakko min wata Choco milo ace ana so nayi biyayya wlh bazan yi ba,Papa yace to dama Bada zuciya daya kace ba ko,nidai irin wannan Papa irinta Inda hali har Sunan so nake na nunawa Yaya Spark Nima fa yes ae,sannan Papa ka bani jari na kirki kaga dai mu a gabanka muka taso Dan Allah kar a barmu da talauci,Papa a dube mu a bamu jari,Papa yace to Arham za a duba ka dinga tuna min yace to Allah ya Kara arziki,Naila tana dariya kasa kasa tana durkushe ta gaisar da Papa ya amsa da fara'a,yace bakya zuwa kwana biyu ki dinga zuwa kinji,Naila tace to,shi Papa ba ruwansa dan tashi kullum azo gidan,Arham yace Papa Dan Allah ka yiwa Yaya Spark fada ya barta tayi karatu,ko bata yi aiki ba ai karatu Yana da dadi tunda dai zamani yazo a barta tayi ko part-time sai ta gama degree dinta a saukake Friday,Saturday Sunday ai yayi,Kuma ma yanzu ga private da yawa ba wahala an gama karatu in da kudi,gaskiya ka fada Masa ya barta,duk su Ikhram tayi degree ita,Chika ta kusa gamawa ga Misam naji yace zai maidata ta karasa ita sabo da mayata ya hanata,Papa yace bai kyauta ba zan Masa magana. Naila taji dadin maganar Arham ya taimaketa sosai yau ya birgeta,suna fitowa tace Inama Zarah kanwata ta girma da na baka ita wlh,Arham yace Bada ni ba baza ku Kara mallake ni ba Kun mallake Spark Nima a shanye ni,a wajen ku zamu kare,wani Jinin zan dakko daban can dangin wasu zan samo tawa,Zarah a auren kauye ta Isa mana amma Bata da kudi,kudin kirjinta basu girma ba wannan ana tabawa zata fara kuka wayyo ka fama min,ka fama min,Naila ta dinga sheka dariya tace Allah ya shiryeka Arham ta juya zata tafi suka ci karo da Spark,yace me kuke cewa haka sai faman dariya kuke Allah yasa ba batsa yake koya miki ba,Arham yace na koya mata ko ta koya min,wurin Papa ya wuce,bayan sun gaisa Papa yace me yasa baza ka bar Naila ta koma makaranta ba ne? Spark yace ni bana so wani Boko,Papa yace a'a ka barta tayi makaranta part-time ma ta Isa a hankali sai ta gama tunda zamani ne ba sai anyi aiki ba, shi Ilimi dadi gare shi,Ya dinga lallaba Spark da kyar ya yarda yace shike nan tunda kace zan sata amma in ana so a bata tsaro, a bani sojoji nata daban su kaita su dakkota,idan Ina free na dakkota na kaita,in sun kaita Kuma su jira a tashi a dakkota,Papa yace wai matarka kai tafi ta kowa ne? ni tafi ta kowa a wajena,karya kake bata fi tawa ba,Spark yace to ka sa Mima na sa Naila aga wa zai cinye zabe,tashi kaje karka dameni Kai kullum bakinka baya rasa magana,ka tabbatar ka sata a school,Spark yace to ya fito Yana Harare Harare ance ya sa Naila a school,yayi niyya su yini amma ya fasa yace taso mu tafi gida ke,ana so a hanani Kwalbewa ko wanne time shike nan kullum na dawo gida matar tana makaranta mene amfanin haka. Naila tana jinsa tayi mukus,yace kinyi shuru,tace ban San akan me kake magana ba,karya ne kin sani kunje Kun hada min makarkashiya wajen Papa,Naila tace ta me? Ni ba ruwana gaskiya,suna komawa gida taga motar da ta zaba dazu a waya,tace wai har an kawo motar, Suna fitowa me gadi yazo ya bashi key din sabuwar motar,budewa yayi ya shiga ya kunna motar yaji zam zam,Naila ta zaga ta shiga gaba tana murna tace munyi mota gaskiya tayi kyau,key din ya cire ya riko hannunta ya sa mata key din a tafin hannunta yace gashi taki ce halak Malak na siya miki,Naila tace na'am? Yace ae taki ce,Naila rasa me zata ce tayi,tace ni Tantiriya yau nice da mota ta fada Jikin Spark. Tace Innalillahi.... Tantiriya tayi mota,Naila da mota,Jamilu Terror wayyo Abba,Yaya Mohsin kuzo,Umma Yarki tayi car sulluwa,Abba Yarka tayi sulluwa,Spark Yana Jin dadi ya gama birge Naila yau,jikinsa ta fada ta kankame shi tana murna,tace babbar yarinya a Abuja za a gatabara kowa ya Adana yaronsa ba ruwana horn da gadara in na sha kwana duk Wanda bai matsa ba babu ruwana,ni da nake da Ashraf Spark,Spark yace ni daina wannan sambatun muje ki bani Bado shine kawai nasan kinji dadin kyautar, Naila tace Kutmar....kai...muje ciki,Spark yayi dariya sai ya tuna sanda take prison yanda tayi maganar sak yanda take yi a prison,tace muje yau har fish style sai munyi,Spark yace a Ina kika taba ganin na kifi? Naila tace na gano ni yau zaka gani,muje yau bado idan zai koma ragadada ba ruwana,Nima yau bani da hankali kawai. Maman Wahida ce ta kira Mero tace zo da Allah ki min wanki,Mero ta kalle ta tace wanki? tace ae ke ba yar aiki bace a gidan Yar uwata,a cikin salary din data biyaki zaki min,Mero tace wannan marar mutuncin Yar uwar taki yo ai ko a iya zagina da tayi ta cinye salary dinta,ke Gyatumar Wahida wlh ko Bata zagina bazan miki aiki ba,bari kiji ko kudi zaki biya ni nafi karfin na miki aiki yanzu,wuuu ni rufa min asiri Ina matar Hanif a nan gidan wa ya isa Dani,ke nifa tun yanzu kallon banza nake wa gandrobobi ma bare ke, kin San da wa kike magana? Kina magana da millionaire Khadija,kina magana da me arziki,Maman Wahida tayi murmushi tace a Hakan? Mero tace da ke zan fara na gane fuskarki duk sanda na tashi maganin mutane Dake zan fara,kin san zan iya kulleki na jefar da key din a kasar nan? Maman Wahida tace Dan Allah jeki karki dameni,Mero tace kin yiwa Kanki gata zan iya zaginki tas wlh ba ruwana ni,Yan uwan naki Yan wulakanci wani dadinsu naji da zan zauna ki more ni,ke nifa me morar jikina yanzu sai Hanif, zan iya tubewa nace Dan Allah Hanif zo ka More ni,Maman Wahida tayi dariya tace ya dirka miki ciki kuwa Kiga mora ta gaske,Mero tace to mene indai Hanif ne ba komai ko yanzu zan iya in haka-in haka ince wuce,Maman Wahida tace ya wuce Ina? ke Yar nan baki tafasa ba zaki Kone" ke Khadija ki kiyayi Maza da soyayya,Mero tace ku sanda kuka yi taku waye yace ku kiyaye? wlh bazan kiyaye ba in tazo kaina na sani na koya daga lokacin na gane karatun duniya,a bari jikina ya fada min,bana so kowa ya fada min gaskiya a kyaleni naji a jikina, Tinkiya aka yanka min da aka haife ni da ita aka rada min Suna Khadija shi yasa dole ku ganni haka to aikin gama ya gama sai addua kawai amma ni ba wani nutsuwa zanyi ba,in kuka ga na nutsu to Tinkiya tayi hankali,kudi ne suka yi gardama maimakon a yanka min ragon da ake layya da shi ana samun Lada sai aka nemo Tinkiya itama tinkiyar tayi ce Bata fara Dan sanin kan duniya ba ta Ina za a ga Khadija dai dai,shi yasa nake wata gilmo gilmo,Maman Wahida tayi dariya son ranta tace Allah ya gyara to,Mero tace Ameen amma a daina neman wani sai na nutsu ni gaskiya,ta juya ta tafi can Inda su Goje suke hada Majalisar su. Mero dakin data fasa ta shiga ta leka ta hango Hanif daga shi sai dogon wando,Jikin Nan mashaallah mulmul,komai me kyau gwanin birgewa,yatsa Mero ta sa a baki tana kallonsa galala,Bai San tana yi ba har ya saka riga,a ranta tace kallo ya kare,a fili sallama tayi taji ya amsa amma ya daga waya Yana magana yace Dan Allah Hajji ka daina maganar Ihsan,ita bata da hankali komai sai an mata,dama ni ba sonta nake ba kune kuka daura aure,tunda abin Nan ya sameni ai bata zo Inda nake ba kuma bata min waya ba,dama wacce nake so zan aura ita Kuma Allah yayi ikonsa,ku kyaleta tayi abinda take so duniya ce,ni dai bazan sake ta ba amma akwai lokaci,Ido Mero ta zaro tace Allah ya Kamaka wlh mugun bakin halinka ya fito fili,dama Kai ba mutumin kirki bane kullum sai mummunan halinka ya fito? Hanif yace ban gane ba?ae ai kace haka mana tunda gashi rannan na zaci baka da aure sai naji budurwarka ta Kone a gobara wannan ban damu ba Alhmdllh tunda ta mutu,yau Kuma na zaci sungul (single)ne Kai" ashe wai sabo da wani abu ma har aure ne da Kai,ai tabarar tayi yawa,lalacewarka har ta Kai haka kayi aure haka. Hanif yace Dan nayi aure shine na lalace ai shiriya ce,idan wata ka aura ba shine yake shiriya amma Ihsan fa,Hanif ya bude baki kamar ta San Ihsan din,yace kin Santa ne? tunda ta aure ka ai dole na ganeta na ganeta,dariya yayi yace to shike nan yanzu me kike so ayi? Mero ta goge kwallarta tace a taimaki ni idan na fita ka kaini gidan Ihsan na zama Yar aikinta,Hanif ya zaci Mero bata San me take harda dariya Yana kallonta a bagidajiya wai zata zama Yar aikin Ihsan,bai san Mero wayo ta hada Masa ba,yace Indai wannan ne wlh zan Taimake ki,Mero tace yawwa na gode ni dama taimakon kawai nake nema kenan,yace an gama zamu je in mun fita ko kin rigani barin gidan nan ai na Baki number ta jiya ki kirani a waya zan sa a aiki aikatau gidan Ihsan matata,Mero tace na gode ta juya ta fito zuciyarta ba dadi tace zaka gane kurenka a kaini can yanda muna tare sai na kwace ka. Mero harda wasu Yan matan su biyu ta ja suka je,tace yau Yan Maza Raina a bace yake harda kwalla,tace kishiya aka yi min,Scola yace ke kuwa wanne Iftila'i ne yake samunki haka Khadija rannan kikace gidanki anyi gobara yau Kuma an miki kishiya, wanne Dan iska ne yake bugo miki waya haka ne? Mero tace sunanta Ihsan yace itace uwar gida saurayina nane,Goje yace shi bai San a cike kike ba,kika ce a cike kike ta ya zai miki kishiya? Mero tace yace sun tsotse kamar alalar Leda tayi gardama a tukunya,Suka dinga dariya,Goje yace ni Ina so da za a jefo ni nan Khadija da a haka zan murmure dake,Mero tace wlh Ina komawa gida sai na sa Babanmu yayi aure,In Allah ya yarda sai anwa Inna kishiya tunda suka ki zuwa kawo min ziyara gidan yari, yarsu guda tana gidan yari sunki zuwa akan kudin mota,Scola ya sheke da dariya yace bankada ta fara, yanzu Babar taki kike wa fata? Mero tace ai duk nasan sirrinta wlh sai na fadawa Amaryar ta kwace Babanmu ya koma wajenta ya juya mana baya duk ya tsane mu kowa ya huta,Goje yace Allah dai ya biya wlh zan so na ganki muyi Ido hudu,Mero tace Kai kwarto ta ido ma ma sai kayiwa mace ciki ni dai ba ruwana da Kai bazan hada ido da Kai ba,idan na fita daga gidan Nan Ina ruwana da ku ma dukkan ku babu na gari i Kashi,kowa Dan iska ne da mummunan laifinsa, yaushe zan hada alaka da ku kuzo Kuna min ture ,Scola yace Jamilu ma ya fita lafiya wlh an kasa yi Masa komai bare ke,Allah sarki Yar uwa Terror Kai mun Sha kallo jiya,Goje yace wayyo Allah ya kwashewa Spark albarkarsa tasss data duniya data lahira duk Allah ya kwasheta,Dan iska Jan banza Jan wifi,fuska kamar kosai,Kai kaga Jamilu Terror lutsu lutsu komai,Balarabe yace ni kadai fa na fara vibration,Ina tunowa na taba rike a hannunta a gidan Nan sai naji wata ni'ima wai nine na taba rike wannan kayan halitta haka, nace ni a barni haka ma ya ishe ni nayi dace a gidan duniya,Ashe ni Balarabe a gidan yarin ma da sa'a nazo. Scola yayi dariya yace ai jiya sai dana ji kamar na tuba daga Daudu wlh da za a bani ita sai na tuba amma tunda bazan samu ba Ina wajen su Hajiya mu'awiya ta. Washer yayi shewa yace jiya idona wlh sun washe ,Mero tace wai Ina Dan Indo ne? Goje yace cab ai Dan Indo yanzu na lahira ya fishi sukuni,Yana can Yana cin ubansa,ai sai ta Allah Kuma,gashi yanzu an bazama neman yaransa cikin sirri duk sai an kamo yaransa da yake sawa aiki ta nan gidan,Sabon hukunci ya tabbata akan Dan Indo,Kaunar Jamilu ta jefa shi a halaka,dariya suka yi Yace ni kaina yanzu buya nake Khadija Baki San case din ba da ni a cikin masu Zane gandrobobi,Mero tace daina buya sunci ubansu,uban gandroba,Kai nifa ba ruwana cin uban kowa nake na baka dama Goje ka zagi duk wani Gandroba kace nice na saka,Goje yace Billahillazi ba ruwana kina katsina Ina daura ko tare muke uban me zaki iya" baki da ko sisi sai surutu. Malam Jilani suna zaune yau a daki yace ohh Kai kaga Jamilu,Malam Garzali yace idan arniyar ce tsab namiji zaiyi ridda a kanta ya koma Krista,ai Ina cikin zikiri Ina zaune na ganta manta me nake karantawa nayi sai dai bakin kawai dake motsi cewar Malam Sharu,ta samu kiwo me kyau,Spark Yana kiwatata gaskiya mashaallah,Kai Kai carkwadi gaskiya ana ci da rabonmu idan wa'adinmu ya kare mu dage mu rangado mata,Malam Garzali yace Kai waye zaiyi sake ai sai na zaba bazan sake ganganci ba irin ta farko salamatu sai na hango fuskar nan tata kamar ta birin turawa wannan Yan karamin,fuska kamar an damko gari. Abba yau gidan Amaryar Jauro yazo,ya iske Jauro an harde a kujera da glass fari medical idonsa Yana karanta jaridar Hausa,Abba yace su Hubby ana ta hutawa,Jauro yace sai yau kaga dama kenan,Maman Annoor ce ta fito ta Sha doguwar rigar atamfa tayi kyau matuka,ta zauna a gefen Jauro tace sannu da zuwa babban aboki,Abba yace yawwa Amarya ya gida ya aka ji da abokina? Tace gashi baka ga ya canja ba ya dawo wani matashi,Abba dariya yayi yace har abada ai yanzu sai dai ki ta tafasa Masa maganin ciwon baya,yau kafa gobe baya na ciwo,Maman Annoor tace a'a banda shi dakau yake shi,Jauro yace fada Masa,ni na taba ganin Aboki Dan bakin ciki irin Hashimu,Suna ma bakin ciki yake an canja min,Maman Annoor tace wai da nace Noori na? Jauro ya sake Jin sabon Suna yace kaji latest ya fito Hashimu,kullum upgrading dina ake,Maman Annoor ta mike tana dariya tace Qalbina bari nazo,Hashimu ya tuntsire da dariya,bayan ta tafi yace wlh yaudararka take idan gaskiya ne Allah ya Maida ni wajen Yar Inna lafiya,kasan Allah Jauro kayi kaffa kaffa da kudinka kodai tana so ta lashe ma kudade ko Kuma akwai manufa ta daban. Jauro ya ja tsaki yace Dan kawai Kai Yar Inna bata fada ma ne mu ai mun Saba Jin sunayen soyayya,Yar Inna nata ba irin wannan bane wlh Yar Inna ta sake tace min Qalbina to lafiya ne,amma na auri Amarya sama ta Kai tace Qalbina to kullum wlh da Ido daya zan dinga bacci nasan da wata a kasa,kaima da Habiba ce ta fada zan yarda amma haka kawai karya take kawai dai so take ta susutaka tunda naga tana da hankali,abinci ta kawo shiryayye iri iri,Abba ya duba yace Amarya me dadin tuwo Ina kallo sai na tuna da girkin Yar Inna na jiya haka tayi min shi, Jauro ya bude baki" yace wlh karya kake Yar Innar Yar kauye me ta iya,teacher ce fa cewar Hashimu,ko ka manta ne teacher ce Kuma tattalin gida take koyarwa har yanzu. AsmaBaffa [2/16, 8:24 PM] AsmaBaffa: 🏫TANTIRIYA🏫 A GIDAN YARI BOOK 3 ~TAIMAKO~ 16-20 Official By AsmaBaffa SADAUKARWA NE GA AIDA MAMAN TASNIM PAGE NAKU NE Binta Abba ~Teemah Hey lovelies Ke matar aure ce kuma kina neman business din dazakiyi daga gida da kuma baya bukatan jari? Kai dan makaranta ne kuma kana neman inda zaka ringa samun kudin kashewa? Ko a'a ke kinada business dinki Amma kina neman wani side hustle haka da zai Kara Miki extra source of income? Ko kinada business idea da kikeson kifara Amma Babu jarin farawa? Toh duk ku tarkato wannan training din, dan ga solution nan nasamo muku, kawai ki danna wannan link din Dan Samun damar shiga group din https://wa.link/49vn47 Jauro ya Kalli Abba Dolo yace bazan biye maka ba,ni ba Kubra bace itace ya zama dole ta dinga biye Maka Banda ni, Abba yace an dora ka a keken bera,ka Sha amarcinka Jauro ni ba wani Abu nace Maka ba,ya maganar zuwan naku Abuja? Jauro yace so nake sai na koma wajen Habiba itama nayi mata kwana biyun ta sai muje kasan mata sai tace sai da kwananta ya zagayo na takalo unguwa,Abba yace ba tace ta baka sati ba,Jauro yace Kai sai na zauna nayi satin? karya take gwada ni tayi,baka San tsiyar mata ba tunda baka taba yin mata biyu ba? Abba yace to ka koma kace ka fada baza ka iya har sati ba tare da ita ba,itama ka zuga mata karya tunda yanzu dama Kai munafukin mata ne,ban gane munafukin mata ba,Abba yace to Nan kazo kace Maman Annoor ba wata kamarta,can ka koma kace ba kamar Habiba ai ka zama Dan iska kawai a gari,ni bazan iya Kara aure ba sabo da dole na Fadi gaskiya,idan naji Amarya ta kwace ni zan fadawa Yar Inna gaskiya nace ni can yafi dadi,idan Yar Inna ce ta kwace ni sai na fadawa Amarya kaga zaman aure bazai yuwu da haka ba ni Kuma dole sai na fada shi yasa gwara na hakura ,suje da kyawunsu da komai zan karasa da na Kubra. Jauro yayi dariya yace dama mata biyu ai sai mu gwarazan Maza. Bayan sati daya Abba da shi za Azo Abuja yace ko Dan yazo yaga gidan auren yarsa ai yazo,Jauro,Annoor,Iman sai Haidar,Jauro duk ya biya kudin jirgi harda Maman Iman Rahma,Abba me 'ya tuni ya fadawa Naila zasu zo da baki,tare da Yar aiki da su Mufee suka shirya girke girke,Spark yau fasa fita yayi,tace baza ka fita bane yau? Yace Ina zanje surukaina zasu zo ai dole na zauna,Naila sai da suka gama komai suka gyara gidan sannan su Mufee suka tafi gida,Naila yanzu har kannen miji ake sawa aiki. Spark driver ya tura aka dakko su har gida,Abba yau yaga gidan 'yarsa,yace Allah ya Kara zaunar da ku lafiya baza ki fita daga gidan Nan ba Naila, Aljannar duniya, da nasan abin ya Kai haka ai kullum tsaiwar dare zan dinga yi karki fito daga gidan nan,Iman tana kusa da Annoor dinta,ita da Babar tata sai kallon kallo sabo da rashin shakuwa,Suna shiga Sanyi da kamshi ya dake su,Naila ta musu sannu da zuwa suka zauna,Abba yace Naila ki rage cin dadin nan kar kiba ta miki yawa ki jawa kanki ya dinga hango Yan shawalwalai,dariya suka yi,Naila tace Abba ni Ina naga wata kiba a haka,gaisawa suka yi da juna sannan ta haura sama ta kira Spark tace sunzo wai nayi kiba Inji Abba? Spark yace to kina ta cin kudina kin hanani Tara abin duniya ba dole ba,dariya Naila tayi ta jawo hannunsa ya mike suka fita,Jauro yace Ashe masu gidan ana Nan Kai sai kace Amarya,Spark ya iso ya gaisar da su da ladabi ya mikawa Annoor hannu suka gaisa,Iman tana makale a Jikin mijinta tayi shuru. Abba yace ya Banga kayan ciye ciye bane ni bana so a sani gaba da magana ko lemo babu gwara a ajiye min abinci a tafi a bani waje,Naila ta mike ta dinga jera musu abin ci da Sha,Abba ya Kalli Spark yace Allah ya Baki Naila Lada ashe haka kike Shan wahala a gidan miji Yana kallo bazai tayaki ba,dama samun miji irinmu a zamanin nan ai sai an tona,Uwarki ta fiki dace Naila data sameni,da nine bazan zira mata Ido ta dinga aiki haka ba,Jauro yace ai yanzu babu irinmu a kasar Nan sai dai ko a Larabawa, Su Annoor suna ta dariya,Maman Iman tace ku don Allah baza kuyi shuru ba agaban yaran ku,Jauro yace a'a bama shuru mu bakinmu kalau yake fes kullum ga brush ga aswaki ta ya za muyi shuru,Spark shi dai dariya yake kawai dan abin na su Abba Dolo sai Ido. Ba ruwansu suka bude abinci sai da suka zaba,Naila tace ko a Kai Dining? Abba yace a'a muna da me ciwon baya Jauro kawo mana abin zama mu a kasa zamu zauna. Naila taje ta kawo musu suka baje a kasa,Iman ta zubawa Annoor su suna kujera,Abba yace ku a sama zaki ci? Annoor yace ya za ayi ta zauna a kasa Iman a'a,Jauro yace Kai yaro munga Habiba ma yanzu ta hakura zama take,Nan wai Kai gyara kake taya matarka? Kayi ka gama,Haidar tunda aka zo aka gaisa baiyi magana ba sai lokacin yace ni ba me zuba min wato ko naci ko na barshi Naila har ta yunkura zata mike kiri kiri Spark ya jawo rigarta ana kallo ya fuske yace zauna,Haidar yace Allah sarki ai shike nan ya zuba abinsa,Annoor Yana ta Masa dariya yace wlh Kuma matata baza ta zuba Maka ko ruwa ba,Abba yace shi yasa naki zuwa da Yar Inna suka kwashe da dariya,Haidar yace ni me zance matarka tayi min Abba ai uwata ce,Abba yace ake kaunar mahaukaciya ma bare tsohuwa da hankalinta,har abada baza ka samu irin Yar Inna ba,ga Maman Iman kaji tarihinta dai to bare dattijuwa irin Yar Inna a kanta sai ka wulakanta budurwa,Spark Yana ta dariyar Abba da son Yar Inna. Sai da suka koshi suka huta sannan mazan suka tafi masallaci Naila ta Kai su Iman bedroom suka yi sallah suka kwanta suna hutawa,Maman Iman bacci tayi Iman ta fito ta samu Naila suna gyara palon da me aiki,ta taya su suka yi wanke wanke suka gyara ko Ina har kitchen,Iman tace Dan Allah Naila kice na kwana a nan gidan kar a tafi dani hotel,Naila tace sabo da me? Iman tace to mijina baida hakuri bazai bari na huta ba na gaji wlh duk ya kashe min kugu,Naila tayi dariya tace zaki Saba ne,ni dai Dan Allah kice zan kwana a nan,Naila tace to shike nan zan gwada,harda bawa Iman Yan tsumi na gyaran jiki ta Sha abinta ta bata wasu ta sa a jaka. Jauro bayan sun dawo daga sallah yace Maman Haidar ta turo min address din gidan su Haidar,Naila tace ni Ina ganin kamar haidar da wani wlh na rasa gidan waye Kuma,sai naga kamar Yana da kanne kamar babu na rasa Inda nasan me kamar sa,Abba yace ai ga address zamu je har gidan,Spark ya karbi Address din ya duba yace a'a to wannan ai gidan su Rafeeq kanina ne,Jauro yace mutumin fa bai taba haihuwa ba,Ae shine fa sunansa Aliyu Shima sunansu Daya da mijin Mummy amma shi ba a kiransa da Aliyu Sunan garinsu ake fada Masa. Yace bari na kira Rafeeq muje gidan kawai ,Rafeeq ya kira suna tare da Ikhram dinsa ya gaji da halinta ya kaita asibiti cikinta ma yafi na Chika kwanaki a duniya,Spark ya fada Masa dai a gurguje,yace to ku sameni a gidan ai kuwa mijin Mama Yana gida yau,suka tafi Rafeeq ma ya tafi da Ikhram can,Spark suka tafi gaba daya,suna zuwa Suka shiga har Palo, Maman Rafeeq Hannun bibiyu ta tarbe su,Jauro yace wajen me gidan muka zo,tace ai kuwa Yana Nan ta mike taje ta fada Masa ta dawo tace yanzu zai fito,ta kawo musu ruwa da lemo. Fitowa yayi cikin shiga ta alfarma Yana tafiya ta manyan masu kudi yanda ya Saba,har ya bude baki zaiyi masifa me ya kawo Maza har palon matarsa baza a jira shi a waje ba sai suka yi Ido biyu da Maman Iman,Baki ya bude mamaki ya kama shi,yace Rahma me zan gani kece? Rahma ta mike tsaye tace nice nan Sudan,Spark yace dama na fada muku da Sudan aka sanshi amma sunansa Aliyu. Rahma ta dafa Iman tace ga Yarka,Maman Rafeeq da Rafeeq suka zaro ido waje,Jauro yace ga Danka Kuma bakin Dan iska tambadadden dattijo,Abba yace a'a Jauro yaransa suna ji kana zagar musu Uba ba dadi,Haidar yace mene amfaninsa ni wlh a Kara Masa wani,a wajen Aliyu Sudan ya durkushe yayi zaman dirshan a kasa ya Dora hannaye a Kai Yana kuka,yace Rahma ki yafe min na cutar dake son ki ne ya sa na aikata miki haka,har lokacin kina halin ciwon hauka Ina ta bibiyar Inda kike har na ganki a kango na da nake ginawa daga nan zuciyata ta kasa hakuri Dake har naci gaba da amfani dake,dalilin sonki na kasa kula da matata ta aure Ina zaluntarta,farko da na fara bataki Baki samu ciki ba sai dai lokacin da kike halin ciwo na hauka tabbas wlh wannan 'yata ce,Jauro yace Kai rufe mana baki algungumi ko kunya baka ji duk mutanen unguwa sun San kaine ka aikata tunda ana ganinka kana fita da ita,Kai rashin Imaninka yayi yawa mace tana ciwon hauka,Rahma ce tayi magana tace sharrin shedan ne laifin kaka ne data Hana shi ni,ni nasan Yana so na,duk ita ce ta jawo min,Aliyu Sudan yace kwarai kuwa. Abba yace to shi Kuma Haidar din fa? Jauro yace ai kasan matar da tazo aiki gidanka Yar wanke wanke da shara Binta,kayi mata ciki kuka koreta Kai da matarka,Jauro ya nuna Maman Rafeeq, kece da laifinki wai ku son miji son aure kar asiri ya tonu Kuna kallo mazajenku suna aikata fasadi sai ku Goya musu baya ku kare zancen to yanzu gashi ke ba take yake ba Kuma gashi ya tara yara har biyu ba yaran sunna ba,ke Kuma Allah bai baki naki ba,mutane baza su hakura da jarabawar Allah ba,Kun cuci yara kawai. Maman Rafeeq tana ta rusa kuka mijinta yayi abin kunya bayan itace ta Kori uwar Haidar tace ta yiwa mijinta sharri,Aliyu Sudan yace yanzu Ina Binta take? Haidar yace tuni ta koma Fatima tana England ta samu hadadde tana aure" jiranka zata yi?,ka daina ce mata Binta" Fatima ce yanzu,Kuma ko tana Nan baza ta aure ka ba,me za ayi da miji irinka,shi yasa kullum na dinga tsallaka katanga kullum son Bariki nake ashe gado nayi ni nasan da dalili,Allah ya kiyaye Yan tabe tabe nayi banyi babban ba adduar Kawu tana bina,Aliyu Sudan yace Nima tawa zata bika,Haidar yace a'a'a ko kayi baza ta karbu ba,irin wannan laifi naka munana Ina zaka sa min albarka ta bini Kai kanka inaga sai da aka sallamaka ka gudo daga Sudan din, nidai kawai ka cuceni,cuta ka gama damu Allah ya yafe Maka,bamu muka yi laifi ba da sauki,takaicin ma da banyi aure ba" da nayi aure ne ma da sauki to ban aure ba wace zata ji Dan shege ta aura,Spark yace Kai in da kudinka ko Yankan Kai kake mata yanzu aureka zasu yi,ni da nake da kanne na baka daya a ciki ko Mufee ko Haly wawarka zasu yi. Annoor Yana jinsu takaici ma ya hanashi magana,yace mudai kawai an cuce mu,yanzu Haidar Kai ubanku Daya da Iman kenan? Yace to ya zaka yi na zama surukin ka,shi yasa muke kama ma,Annoor ya Kalli Haidar ya Kalli Iman yace Kai ya Akai ban kula ba sai yau Kuma Kuna yanayi fa,Haidar yace sa wasa yaro,Haidar ya Kalli babansa yace to yanzu Kai Baba zamu ce ko me kasan bamu da gadonka sai a bamu rabonmu tun a duniya,in kana so mu ce Maka Baba wlh in baka so to kaje da kudinka ni dai ba sake Ganina zaka yi ba dama can Ina da Ubana daban me zanzo nayi Maka,uwar tawa da ka koreta Gombe garinsu,Aliyu Sudan yayi mukus kunya ta isheshi. Rafeeq yace abin kunya ya bar gidan su Spark ya dawo gidanmu,'Ya'ya biyu rigis ba aure aka same su,sai nayi wata ban zo gidan Nan ba,dama Nima ba kaunata yake ba tunda aka kawo ni riko ka tsaneni,kwana a gidansa bana yi sabo da ba shi ya haife ni ba,matarsa duk kyan gidan Nan abinci wahala yake mata,badan ni ba da yanzu ta canja kamanni,dama shi yasa ake so mutum ya shuka Alkhairi in kaki Kuma duk sanda Allah ya Kamaka to wlh shike nan Kuma,yanzu gashi iya wannan ya isheka,ba duka ba zagi asirinka ya tonu a idon duniya,ga hakkin yaranka,hakkin matan daka zalunta,hakkin matarka ta sunna gani ni kaina Dan riko hakkina kadai sai yasa asirinka ya tonu,yanzu ni uwata zaka sakar min mu ware tunda ba sonta kake ba dama ga Rahma ta dawo ka aureta ka sakar min uwa wlh. Spark yace wlh kuwa ka saketa kawai kanwar uwar mu a saketa mu tafi da abar mu,Rahma tace in aka saketa Nima bazan aure shi ba Dan Allah kuyi hakuri zai gyara halinsa sai mu zauna lafiya mu hada kanmu,Maman Rafeeq takaici ya kamata tace wato ita wannan kawai ma tunaninta aurensa zata yi ta shugo gidan sabo da so,ni na hakura da Kai Aliyu Sudan ka Aiko min da takarda ta sai na koma gidan Rafeeq,Rafeeq yace gidan Mima zaki zauna gidana bazai zaunu ba,gidana ba gidan zama bane Mama, mu kin San ba a rabamu da Uhum hum,daki ta shiga Aliyu ya bita Yana Bata hakuri ta fito da akwatinta. Spark yace ni Ashraf na kashe auren kanwar babata yau mutafi gida kina da gata muje ku hadu ku uku a gidan Mima kwana Nan uwata zata tafi babban gida,Haidar yace ku tafi da ita wlh kar ta zauna karku yarda sai ya bata Jan kati uku. Abba yace Dan Allah ku zauna,Kai Ashraf ku tsaya,suka tsaya Shima Aliyu Sudan din ya zauna ya nutsu Yana kwalla,Abba yace duk wannan abin babu abinda zai gyara ayi hakuri a tattara a yafi juna babu abinda ya Kai hakuri riba,Kai tunda kasan baka son matarka na mene zaka takura mata ka barta ta samu Wanda ke sonta,ka auri wacce kake so kaima shine zaman lafiya,da ka auri wacce kake so duk baza ta kaika ga aikata wannan cikin shegen ba,yace Nima iyaye ne suka hada,Maman Rafeeq tace Nima na tsane shi ba sonshi nake ba sabo da abinda yake min bana kaunarsa" kawai ya sake ni ya auri wacce yake so final Jauro da Abba suka zauna suna ta sasanci Abu yaki yuwuwa,Maman Rafeeq tace ita tana jiran takarda,Ikhram tana ta kallon Haidar tasan tarihinsa yayi kama da Wanda akace sun hadu ta bangaren uwa,magana tayi tace Haidar Dan Allah a Gombe su waye danginka? Jauro ya karbe zancen ya bata labarin dangin tace to wlh shine cousin dina da babata da babarsa uwarsu Daya ubansu daya ita babata ta rasu a prison,ka kira Mamanka kaji,Haidar yace Kai karfa a dinga gayyato min Yan uwan da ba nawa ba sabo da ni Dan gaba da fatiha ne kowa sai yace Dan uwana nane,ya kira Mamansa tace Haidar kunje kuwa? Yace ae an gama komai zan Baki labari ga wata Ikhram wai yarki ce Yar gidan Sarah wai wacce ta rasu a prison,Maman Haidar harda kuka tana Allahu Akbar Allahu Akbar bani ita 'yata ce,Rafeeq yace to fa Yan uwantaka ta tafi tayi naso harda Ikhy dita. Sun Dade suna waya da Ikhram,Jauro ya mike yace ku tashi mu tafi sauran bayani ya rage gareka Sudan in ka yanke hukunci ka tuntube mu,suka mike suka fice ya biyo su ya karbi number waya kunyar duniya ta ishe shi,Abba yace ba Sudan ba ko Makkah ne Kai ba ruwan mu. Gidan Mima suka dunguma,Mima Taga sabuwar masifa Kuma again kanwarta itama wata ta afka wani hali,Mima tana Jin komai ta dinga salati tana sallalami,Mummy tace ni gwara ma na bar garin Nan na huta da wannan masifa,Arham yace saura kis ai jibi za a fara zama,tace zanci ubanka wlh,suna zaune Mufee ta fito cikin atamfa fitted gown ta zuba kyau gasu da kyau dama,Haly ta fito suka gaishe su Mima an koyawa yara gaisuwa,suna tafiya Haidar yace a ransa ba ruwana Ina Dan shege wa zai bani yarsa,kuje da kyawunku bazan so kowa ba,Jauro ya Kalli Haidar yaga Yana kallon Mufeeda,Jauro yace karka bada mu mana,Haidar ya fuske yace ni me nayi suna Kus Kus,Mufeeda Kuma su Haly anga zuka zukan samari harda nutsuwa,ana nuna halin kwarai. Mima sai yau taga Baban Naila,tace Inshaallah zamu zo har gida a gaisa,Abba yace Allah ya kaimu,Papa yazo suka gaisa a ranar su Abba suka ce sai dai a kwana suka koma gidan Spark kafin su tafi hotel,Naila ganin su Jauro sun fita sai Haidar, Annoor,Iman Spark da ita tace amma a Nan zaki kwana ke Iman,Iman tace ae mana ai ni Ina Nan,Spark da bai San zance ba yace mata da Mijinta ki raba su Ina ruwanki wannan ai shishigi ne ko ke kadai kike kwana ke? Annoor yaji dadi yace so take ta rabani da ita yau Yana dariya,Spark yace a'a idan anan zata kwana Shima ya kwana anan,Annoor yace shine maganar gaskiya,Iman takaici ya kamata da bakin cikin Spark,tayi shuru tana fushi,Haidar Yana jinsu yace ni yanzu Yaya ne bazan ce komai ba kanwata ta rainani,kaji da shi dan iska cewar Annoor. Naila ce tayiwa Spark rada tace Kai baka gane ba Baby hutawa fa zata yi ya dameta da naci baya bari ta huta shine zata kwana a nan yau,Spark baiyi kasa kasa da Murya ba yace to kawai sai ta huta? akan me zata huta?..Baki Naila ta rufe Masa da hannu,Annoor yace na gane kan zancen Kuma ai,ya leka fuskar Iman Yana dariya yace baki kuka hada ashe, Spark yace karka biye mata Dan Allah indai mata ne haka suka ke,kafin ayi abu suna wani nokewa ana farawa Kuma sai....Naila ce ta rufe Masa baki tana dariya tace wai mene haka Dan Allah ka kyale yarinya a barta ta huta,Annoor Yana dariya yace bamu zo duniya Dan mu huta ba,bauta aka turo mu muyi sabo da haka ita muke yi. Washe gari tun kafin su tafi Aliyu Sudan ya nemi su Haidar ya sake Bada hakuri sannan yace dukkan abinda ya mallaka ya bawa Haidar Rabi Iman ma Rabi,ya dauki iya harkar business dinsa shi zai ci gaba da neman kudinsa amma kadarorinsa duk ya damkawa Haidar da Iman takardu kowa da nasa,Haidar yace shike nan na yafe Maka" Baba Dodar har lahira,Iman ita duk basu dameta bama iyayen tunda taji shirgin ba raga ta rabu dasu Uzurinta take to taji suna son juna duk da haka harda batun aure su cikin shegen ma bai dame su ba ta soyayyar su suke. Yau suka koma gida yace zaizo har gida cewar Sudan. Suna komawa Kuma Baban Annoor yazo shima Yana rokon Annoor ya yafe Masa Annoor yace tunda ka haife ni ta hanyar aure ai ni ka gama min komai na yafe ba abinda ka min wlh,yace to Yar uwarka fa Maryam ka yafe mata,Annoor yace wannan Kuma bata Isa ba tunda ta sa nayi Zina bazan yafe mata ba,yanzu da kanwata ce uwar daya uba daya da shike nan,sannan ta min asiri bazan yafe mata ba,aka buga aka buga akan Annoor ya yafe yace bazai yafe ba,Iman ma haka ya zugata yace wlh in kika yafe munyi hannun riga da ke,Baban Annoor yace Inshaallah watarana zaka yafe mata ne,Annoor yace to ban sani ba ikon Allah amma Banda yanzu bazan yafe ba. Nabeel sai dai a bashi labarin abinda ke tafiya Yana gida abinsa wajen Hidaya Yana jinya,sai da ya daga mata kafa ta warke sannan ya sake nemanta ko hanashi Bata yi ba sai abinda yace da ita sai yanda ya juya ta,in yace kaza shi za ayi,tafi Naila Jarumta sosai bata raki,fitowa tayi daga kitchen da plate tana tafiya a hankali sabo da ta Sha wahala jiya a hannunsa,fitowa tayi tana kiran su Zarah Dan Allah su zo ace duk sun ki zuwa gidanta tunda aka kaita,Nabeel yace da kaina ma zan dakko miki su ai,Dan Allah ka dakko min su yara baza suzo suga Yar uwar su ba ana ta gasa mata Aya a hannu,dariya Nabeel yayi yace wacce Aya na gasa miki a hannu daka jiyar Dake dadi,Wahala dai ka Jiyar dani ta zauna a gefensa tare da Dora kanta a kafadarsa suna Hira. Beauty ganin ba kowa sai ita a gidan ga gidan part biyu tsoro taji tace karfa ya karo kishiya yaga waje available ba komai a ciki,Chika ta kira a waya tace Chika nifa part din Hanan data bari Yana bani tsoro ya taba yin mata biyu kar yaje yaga fili a banza ya Nemo wata,Chika tace na dade Ina wannan tunanin tun wuri kisa a hade part din nan da naki tunda ba Nisa ki samo me zanen gida ya zana gidan yanda za a hade ya koma part daya kawai sai ki nuna Masa nasan zaiyi,ko baiyi niyya ba da yaga nonuwa ai shike nan,Beauty tace me kika Maida shi shike Nan daga yaga boobs wlh Kun Raina mijina ke da Naila,Na kusa haihuwa Kinga kafin na haihu sai a hade part din,Misam Yana jinsu suka sako labarin motar Naila da aka siya mata,bayan sun gama waya Misam yace ke da Ikhram naga Kuna son motar Nan ta Naila ba ruwanku ku ko kishin faccalancin ma bakwa yi,ku dinga yi mana Dan Allah mu fara sasanci,ko sai Nan gaba zama yayi zama ne? ance faccalanci yafi kishiya masifa,Chika tace sai kace jahilai kowacce da Mijinta Kuma ko wacce muna da rufin asiri wa zaiyi wani faccalanci,Kun taimaki kanku Dan wannan abin takaici ne faccalanci a dinga kishin ko wacce mijinta daban ai aikin banza ne,kinji abin kunya ya fada gidan su Rafeeq Uwar goyon Rafeeq Kuma itama aurenta Yana ta karkarwa Yana rawa ,Chika tace naji labari Ikhram ta fada min Haidar dinma Dan uwanta ne,Misam yace Allah ya taimake ni na gama karuwanci na lafiya na fita lafiya daga Bariki,Chika tace daina zancen nan please, yace har yanzu in na tuna sai nayi nadama,Chika tace sahihin tuba kenan haka ake so nawan me Hallaren da Madara,murmushi yayi yace kwana Nan zamu dinga shiryawa Naila makircin Dani miji ni da Rafeeq,wannan gatan ya mata yawa ta mallake mana dan Uwa,Chika dariya tayi tace kunyi a banza. Beauty kuwa me Zane ta samo kwararre yazo yaga gidan ya zana yanda zai koma ta biya kudade masu tsoka ta karbi zanen tace sai na nemoka,yace ba damuwa,sai da Mohsin ya dawo yayi wanka ya shirya yaci abinci suna kallo,hannayensa a cikin rigarta yana sarrafa na shanunta ta jawo zanen ta nuna Masa tace Kalli gidan nan da part dina da waccen part din a hade su kaga Nan wani corridor ne zuwa kofa,Kalli nan Palo,Mohsin yace wow yayi kyau ai yafi kyau ma gidan a haka,Beauty tace so nake kafin na haihu ka gyara min,gyaran ai kadan ne babu yawa ba wani kudi za aci da yawa ba,in da hali Please. Mohsin bai kawo da manufa take so a canja tsarin ba,yace shike nan amma kin San na kusa tafiya Saudiyya ko,karka damu ai lokacin na haihu,wai ba kudi bane za a samu,ni bazan karbi kudin kowa ba da nawa zanyi amfani,lallai tun yaushe Naila tana ta kawo ajiyar dollars har ta hada kudin wajen 500usd tana Nan a ajiye Kuma zata karo wasu kawai kayi min ginin nan ba wani kudi za aci ba,in Kuma ba damuwa ni Ina da kudi zanyi,yace a'a bana son kwandalar mutum a gidan nan zan miki ai,tace thank you lokacin na haihu an gama,yace yeah za'ayi inshaallah. Mummy bayan kwana biyu aka fara zaman kotu Spark kin zuwa yayi Sam,su Misam ne suke zuwa,lokacin Alkali rana Daya yake saurarar karar Mero da karar Haneef,kusan tare ake kawo su kotu,gidan yari sosai suka tsayawa Mero,sai da aka dawo kan batun Naila amma sabo da Spark ya gama biyan kudi in akace case din za a dawo da shi sai an kama Naila akan ta gudu daga gidan yari sannan Kuma ta shiga wajen Maza a suffar Maza shi yasa aka kashe case din,Mummy ko sharia bata wahalar ba ta amsa laifinta gaba daya har kashe mijinta da tayi. Mima sai kuka suke yi sun San itama Mummy sai taje gidan yari,amma Mummy ita ta hakura ma ko kuka bata yi ta saduda tasan ya zama dole ta daure zuciyarta. Duk da haka Alkali Bai yanke hukunci ba ya dage sauraron Kara sai nan da sati biyu lokacin zai yanke hukunci gaba daya,sannan ya Bada dama ayiwa Mummy gwajin kwakwalwa. Mummy tace ni kalau nake wanne gwaji za a min Ina sane nayi zuciya ce ta kaini me yayi saura, Alkali ya gama Kuma ya zama dole tunda Mummy har an tsareta itama a layin su Mero. Mero suna komawa ciki ta wuce makaranta ta dage sosai ba dare ba rana karatu take,Azima ta sameta tace ke Mero wai me ya sameki kamar me aljanun karatu,Mero tace tunda na samu na Sallah da sauransu ai na Kara da Ilimin zaman aure ko,ai Nan tarihin magabata nake bibiya naji Yaya suka yi zaman auren su na samu nayi koyi da su,nidai gaskiya hakurinsu yayi min yawa bazan iya ba uban kishiyata zan ci ba ruwana,Azima tayi dariya tace au nan Haneef din zaki aura? Mero tace Ras ma kuwa ai in kika ga ban shiga ba na kwana da shi a gado daya ba to Allah ne baiyi ba sannan ba Sunan uwata Jummai ba,ai Inshaallah sai naga Ijakala babu wando,Azima tace wayyo Khadija tana dariya tace Ijakala har kin riketa Dattijai ne fa suke fada a gidan Nan,Mero tace tafi min dadi a baki,taci gaba da karatunta na tarihi tace muje yau akwai tarihi,kina gani na kusa barin gidan nan shi yasa nake dagewa na koyi abinda zan koya,yau Malam ya shiga uku da tambaya duk abinda ban sani ba sai na tambaya. Kwana wurin biyar Mero bata je wajen su Scola ba tana ta karatunta na addini littafan iri iri,da koyon wanka harda kwalliya dauri duk koyo take,indai Mero taga kin iya Abu to sai ta Allah ta dinga naci kenan sai an koya mata. Su Spark kuwa bikin Kamal suka Sha aka gama lafiya. Mero yau taje wajen su Scola,tana magana Goje yace I miss you,Mero tace tab zaka cuci kanka wlh dan na kusa barin gidan nan,Ina fita Kuma aure za ayi min ko gidanmu bazan zauna sosai ba zan kama gaba na,Balarabe yace a'a Dan Allah Khadija karki tafi zamu yi rashi,Mero tace kanwa na kawo kuci gaba da dakon soyayyar Naila Tantiriya,Jamilu Terror ko? Goje yace Allah sarki ai ko su Malam Sharu wlh karya suke suna kaunar Jamilu ba wani Imani,suna wani kasa kasa da kai karya suke son Jamilu suke,ana magana suna subhannallah Subhannallah,Scola yace Malam Garzali fa idonsa har ja yake sabo da kallon Naila Ina kallonsa Bai San Ina kallo ba,Goje da tausayi yace yanzu spark nasan ma yayi mata ciki,Balarabe yace ai ni gaskiya fatarta ta me ciki ce,Scola yace wlh tsabar Jin dadi ne sirrin 'ya mace na 'ya mace ne ni na gane kawai hutu ne ba ciki ba. Mero kwana biyu bata Jin motsin Haneef sai da ya rage saura kwana Daya a yanke hukunci Mero taje tace to sallama nazo ko ka rigani fita ko na rigaka,ya alkawarina? Haneef yayi murmushi yace Yana Nan alkawarinki,tace to sai ka jini yace shike nan har kin tafi? tace ae karatu nake yi,yace bye ta furta bye bye ta fice. Washe gari zaman kotu na karshe,gwajin Mummy na kwakwalwa ya nuna lafiya kalau take Alkali ya yanke mata hukuncinta na daurin shekaru Hamsim a gidan yari,Mummy tace kawai kace daurin rai da rai a shekaruna a Kara Hamsim ai bana raye wannan ai bakin munafurci ne ta furtawa Alkali kiri kiri,yayi shuru ya kyale ta,tace Kaine zaka ja kwana na zaka ce Shekara Hamsim kaima kasan karya kake lokacin bana raye,kawai in zaka ce daurin rai da rai kace za a mana iyayi,makarantar legal din da kayi,legal fa kayi,Alkali yasan zafin hukunci ne Suna Haduwa da haka Bai ce kala ba ,kotu ta wanke Mero fes aka sallameta,suka fito suna Murna,Mummy aka tafi da ita ciki,su Mima sai hawaye suke yi,Mero ta fito tace ko ciki baza ta koma ba gida zata tafi. Dukkan dangin Mummy suka tafi ba Wanda ya kula Mero ciki,Spark bai zo ba ma sabo da kar yaga bacin rai dan zai iya kuka Mummynsa guda. Mero fitowa tayi dama ta karbe ragowar kudinta dubu ashirin na asusunta tsayawa tayi jiran shari'ar Haneef tunda harda shi yau,ba a dade bama shi gaba daya aka kashe case dinsa cewar ba shi ya batar da yaro ba bincike ya nuna yaro Yana Lagos ma ya tafi neman kudi an ganshi a Lagos. Tana tsaye sai ganinsa tayi ya fito shima,Yan uwansa sunzo,Mamansa ce bata zo ba amma mijinta yazo,suna ta tayashi murna,Mero ya kalla ya karasa Inda take Yana murmushi yace to sai a koma gida aci gaba da tace gasara da skirt,dariya tayi tace to yaushe zan fara aikin? yace in kin shirya ki min waya,tace to yace ashe dai kina da kyau,Mero tace da me ka dauke ni,ta juya ta fice,Shi kuwa mota ya shiga cikin Yan uwa suka ware,Mero Napep ta shiga ya kaita Tasha Inda zata hau motar garinsu,tana zuwa ta samu Napep har kauyen su ta shige. Spark kuwa tunda yayi waya da Mima ta fada Masa hukuncin da aka yanke duk da ya San zai faru sai da ya shiga damuwa,Yana Office gida ya dawo jikinsa a sanyaye ransa babu dadi,Naila tana Palo tana danna waya ya shugo,ta ganshi wani iri tace wa ya taba min Mijina? Mikewa tayi tsaye ta rungume shi,kankameta yayi kawai taji Spark Yana kuka,Naila bata San an yankewa Mummy hukunci ba,sai da taji tsoro ta janye jikinta da sauri ta rike hannayensa tace lafiya? Me ya faru? Baby mutuwa aka yi? yace Mummy ta tana gidan yari live in prison,Naila tace oh my God Baby I'm so sorry,Allah yasa wannan hukuncin ya zama silar shigarta Aljanna, Inshaallah baza ta Sha wahala ba ai VIP za a Maida ta ko? Naila ta sa hannaye ta goge masa hawayensa tace ai ba mutuwa tayi ba Baby,kullum in kana so zaka je ka ganta ko? Naila harda hawayen karya wai Dan ta nuna ta damu da damuwarsa, tace gobe ma zamu je ai ko duk abinda take so za a bata. Rafeeq ne yazo gidan yace Spark kayi rashin Mamanka,tashi yayi ya haura sama kawai kar ma a dame shi zai iya yin kuka a gaban mutane. Naila tace Kai fa kuka yake baka sani ba,Rafeeq yayi dariya yace Spark da kuka cab,sai kace ta mutu,waye yace tayi kisan Kai,abubuwa ma iri iri duk tayi Kuma yasan hukuncin nan mene abin kuka kawai shagwaba yake miki sabo da kina lallashinsa,naga mota Allah ya sanya Alkhairi,Naila tace Ameen,yace kin fa ishe mu kin kankane mana kayan Dan uwa,Dariya Naila tayi tace Dan bakin ciki sai dai ya mutu,Rafeeq yace zaki ga makirci,Misam ne ya dawo daga kotu yazo direct Shima wajen Spark. Yace Ina Spark Dan wulakanci sai yaki zuwa,Rafeeq yace kuka yake Yana daki,Misam yace Allah sarkiyiyiyiyi...dole yayi kuka wlh tunda aka tsige shi a nono aka bata,Kai Spark yasha gata a duniya gaba daya Bata bari ya rayu a kasar Nan sosai ba,taje ta tare da shi a kasar waje yayi karatu ta sakar Masa kudi sai da ya zama me kudi ta ko Ina,Kai ku kyale shi yayi kuka Dan Allah. Ke Naila sai na ganki a nan kije ki kwalbe shi wlh ras zai dawo karya yake,in ya Kara ko kwalla Allah ya bani abinda nake nema cewar Misam. Naila tace space na bashi naga Yana bukatar a barshi shi kadai,Arham ne yazo yace Kuzo ku taimakeni,sai da ya basu tsoro sun zaci wani Abu ne,yace Papa ya kashe ni wlh ya zabo min wata aladiya Kuma wlh wai sai na aure ta ni ban isa aure ba,a fada Masa ban balaga ba,ya samu waje ya zauna ya zuba tagumi,Rafeeq yace Kai har gata ne da Kai haka sai an zabo Maka mata? Misam yace Kai ba dai wannan Basma ba ta kauye? Na ganta an kawota Papa yace karatu zata yi a Nan,Arham yace ita ce,wannan kucakar,wai na Kai Masa samfur din Naila wai ai yaga itama fara ce yo ni fari nake so Nima ai fari ne,yarinya sododuwa, Rafeeq ya sheke da dariya yace ya batun kudin? Arham yace na gagara ganewa kirjin Maza ne ko na mata,kawai an dakko min mata Maza,Misam yace a'a Arham wlh karya kake wannan yarinyar kace kawai Yar kauye ce zan yarda amma tana da komai me kyau wlh,Arham yace Kai nifa nono inchi inchi ba Wanda ban taba naji ba,ta ya za ace a nan kirjin wata Basma akwai shi,ai Kai Misam ka Saba Bariki kowa me kyau ce a wajenka dole kace haka,Ashar Misam ya dura Masa yace Dan uwarka ba na tuba ba Yar ubanka na taba yanzu. Ai abin Yana jininka ni dai ku fadawa Papa kawai ya canja min wata,yace bazai canja ba ya riga ya sanar da iyayenta aure ba fashi,dama Kai Dan Iska ne Arham mata kake tabawa kirji? Arham yace duk Yan ajinmu kowacce naji nata,yanzu dai nayi aji class ne dani ba na kowa zan kula ba,amma ni wlh duk Wacce bata da shi bana so,ya zauna ya zuba tagumi,yace ni da nake so a samo min wacce kamar zan hau na zauna a kai sai a dakko min allo,kaje ka fadawa Papa mu ba ruwanmu cewar Rafeeq,Arham yace cewa yayi fa zai sa a kulle ni a guard room dole sai na aure ta ya Ilahi ni ba girma nayi ba,na mene ake gaggawa sai an kaini dakin aure. Misam ya sheke da dariya yace kar ma a turoka Office dina aiki,ni da an bani jari zan tsaya da kafafu na me zanzo wajenka nayi,ni da Shaheed an bamu jari an kaimu kasuwa an gama mana komai farawa kawai zamuyi,yanzu koya ma mukeyi har motoci zamu dinga siyarwa,to kaje ka fadawa Mima ta rokar ma Papa a canja,Arham yace dariya take ta yi tana murna yanzu yarinyar ma kaunar ta take yi har da yi mata kitso yau fa,nidai Ina zan sa kaina bakina ya ja min. Har su Rafeeq suka tafi Arham yace shi bazai koma gida ba yayi yaji,Naila tace to ai mu Nan akwai wajen zama Arham abinci Yana kitchen bari naje wajen spark kuka yake,Arham yace kuka Kuma? Sabo da Mummy? tace ae yace Dan Tani su jefar da mukullin gidan yari a teku,zanyi dai dan missing dinta kadan tunda Ina more cinyarta watarana,jeki kina bashi Uhumhum dinsa zaki ji luf wlh karya yake so yake ki bashi hakkinsa cikin sadakinsa,Naila tace Allah ya shirye ka ta haura sama tana dariya,Arham yace ga samfur an Kai sabo da idon Papa yayi shutdown shike nan sai ya dakko Basma daga kauye,kauye fa... Naila tana shiga ta samu Spark a kwance yayi shuru Yana tunani cikin damuwa,a gefensa ta kwanta ta fara lallaba shi sai gashi ya bige da romance ya daina kunci... AsmaBaffa [2/18, 7:33 PM] AsmaBaffa: 🏫TANTIRIYA🏫 A GIDAN YARI BOOK 3 ~TAIMAKO~ 21-25 Official By AsmaBaffa SADAUKARWA NE GA AIDA MAMAN TASNIM Page naki ne Iya2 Hey lovelies Ke matar aure ce kuma kina neman business din dazakiyi daga gida da kuma baya bukatan jari? Kai dan makaranta ne kuma kana neman inda zaka ringa samun kudin kashewa? Ko a'a ke kinada business dinki Amma kina neman wani side hustle haka da zai Kara Miki extra source of income? Ko kinada business idea da kikeson kifara Amma Babu jarin farawa? Toh duk ku tarkato wannan training din, dan ga solution nan nasamo muku, kawai ki danna wannan link din Dan Samun damar shiga group din https://wa.link/49vn47 Spark yaji Naila a jikinsa,narkewa yayi Yana shagwaba kamar yaro Dan yaye,duk ya makalkaleta Yana cewa Mummy ta tana can,Naila tana lallaba shi tace kayi hakuri zamu je ko gobe ka ganta normal,zata saba inshaallah,Yau zata yi Kwanan wahala ya furta,Naila ta gaji da korafin Spark yaki yayi shuru,ta hau romancing dinsa tace a ranta bari na gwada maganar su Misam,na tafi ace baka damu da miji ba, daga Dan fara kiss sai ga Spark ya zake,Booby daya aka sa Masa a baki tuni ya manta da wata Mummy a prison kamar Wanda aka Masa Allura ya watsake,Naila tace eyya bama ka Jin karfi a bari later kwanta ka huta kaji,muryarsa taji yace da karfi na zan iya komai ma,dariya tayi tace au da karfinka? Yace sosai . Mero tana Isa gida sai Ganinta aka yi tsidik a cikin gidansu na bulon siminti ne amma kamar kango haka yake,wani tsohon rubabben gini ne tun ya zaman,dakuna uku ne a gidan sai kitchen din langa langa na karfe sai toilet,Inna ta iske a kitchen tana aikin soya awararta ta yamma,Mero tayi Sallama ta shiga,Jummai ta leko tace ya naji kamar Khadija,Baki ta bude duk taji kunyar yarta ta kasa zuwa su ganta a gidan yari,tace wani satin muke cewa zamu zo Khadija Ashe kina tafe,Munnir da ya fito daga daki yace wlh da kudi Yaya Khadija cewa tayi baza su ba tsada tayi yawa. Mero tace ai gani na dawo,Jummai ta fito daga kitchen tace ya akayi na ganki Kuma? gudowa kika yi? Mero tabarma ta dakko ta shimfida ta zauna tace a bani abinci naci tukun naci na huta sai naji dadin labari,Ina Abbu? ya fita kasuwa,Jummai kitchen ta koma ta zubawa Mero shinkafa da wake da Mai da yaji ta kawo mata ta kawo mata awara a plate tace Kai Munnir ebo mata ruwa,Khadija ta zauna ta fara cin abinci sai da ta cinye komai tas ta Sha ruwa sannan bakinta ya bude,Abbu ne yayi Sallama ya shugo suka amsa,Baki ya bude ganin Khadija a gida,yace ya aka yi haka ta faru? Farin ciki ya kama shi ya washe baki yace Khadija kece? Mero tace nice mana da baku zo ba gashi na fito,wai ku haifi 'ya a cikinku amma bakwa sonta haka ake rayuwa,kudi yafi da,Kun San bakwa son yara baza ku iya kula da su ba kuka haifo mu,Allah ya dube ku ya Baku yara biyu kacal amma baza ku iya rike su ba,sabo da son kudi,Abbu Murya a sanyaye yace wallahi tallahi Khadija ba laifi na bane laifin Jummai....Jummai itace mijin ko Kaine Abbu,ka zauna tana gara ka kamar tayar mota" ka karo kishiya mana kayi aure,yo magana ta Allah fa,Jummai baki ta bude tace Khadija ni kike cewa a karo min kishiya? Abbu yace kwantar da hankalinki Jummai bazan ma iya yi miki kishiya ba,Mero tana jinsa takaici ya kamata sosai na halin mahaifin su,Jummai tace tunda halinki zaki dawo da shi na fito na fito da ni akan ke sai kin koya min zaman rayuwa to wallahi ki koma aikatau,ya zama dole aikatau zan kaiki tunda samarin ma ke ba kula su kike ba bare ace za a miki aure to dole ki koma aikin wanke wanke da shara domin ki samo mana kudi,idan ba haka ba wallahi da katifa za a kaiki gidan miji,Khadija tace a kaini da abinda Allah ya hore,Abbu Yana ji Yana gani yayi shuru baya ko magana. Jummai tace to gidan aiki zansa a sake samo miki,Mero tace na samo ma wlh a Kano Inshaallah gidan me kudi ne har gida za a zo a dauke ni,Inna sabo da sakaki ko a jikinta babu ruwanta da waye za a je gidansa burinta a samo mata kudi,Baki ta washe tace Allah ya kaimu Khadija Allah ya miki Albarka,ki bari ki huta ki murmure tukun,Kai Munnir zo kaje ka siyo mata kifi taci taji Dan dadi dadi,Sani uban Khadija Yana kallo Yana Jin haushi amma bazai iya magana ba,da kyar yace Jummai da dai an barta a gida ai Ina ga zai fi ko? Shawara na bayar ba umarni ba a dai duba,na yarje mata ta tafi baza ta zauna a gida ba mene amfanin Hakan,to shike nan Khadija Allah ya tsare ki kula kinji,ki tsare mutuncinki a duk Inda kike tunda kinji dai Hajiya Jummai ta gama magana. Khadija takaicin Abbun su ya kamata ayi mutum kamar ba mutum ba,a ranta tace anya kuwa Abbu mutum ne? Suna haka wata bazawara ta shugo gidan Zuhuriyya Yar babba ce haka amma ba can ba baka ce kyakyawa Yar Fulani,kawar Jummai ce kut da kut,Abbu Yana kallon Zuhuriyya ta shugo ya mike Tare da gyara sallayarsa a bakin kofa ya tada Sallar Nafila ta dole ya dinga Sallah ba ji ba gani,har sai da Zuhuriyya ta gama abinda take ta tafi sannan ya sallame,Khadija tace Abbu meke nan Hakan? yace hanyar lafiya a bita da shekara Khadija kar ma mace tace ni Sani na kalle ta,ba ruwan Sani da mata,Mero shuru tayi tace ita Aunty Zuhuriyya din ai Abbu ta kirki ce,kana gani kullum shawara take bawa Inna tana nuna mata hanya Ina ruwanta da Kai,Kai da ake so ka zama mijin mace hudu,Abbu yace mace hudu Khadija? Jummai Kuma inyi ya da ita? Itama tana cikin matanka Abbu,a'a Khadija barni da ita din kawai,uhm uhm Abbu yanzu yayin mata biyu ake shine gayu shine cinyewar,yace a'a ba ruwana ,Innar su Khadija tana kitchen bata San me suke ba. Mero tunda ta dawo mutanen garin suke cewa Yar mace ta dawo, taki aure ta gandame a gida bata da me aurenta,ko ta kansu bata bi" haka tayi sati guda duk kauyen ya isheta tace ga Inda zan ta kallon Yan gayu da wanka ko ta Ina,ko ban samu samu miji hadadde ba ai yafi min akan zaman kauye. Waya ta samu ta Nemo karama ta siyeta dubu hudu ta sa layi ta kira Haneef,tana shiga amma ba a dagawa, yini tayi tana kira ba a dagawa,da dare ma da ta kwanta haka ta dinga gwadawa amma ba a daga ba. Bangaren Haneef kuwa tunda gidansa suka nufa direct matarsa Ihsan ya samu a katafaren Palonsa tana zaune ta Sha gayu cikin kana Nan kaya riga da wando tight milk and brown,ta Sha hular gashi me kyau tare da Dora Yar facing cap a kanta,tana latsa wayarta me tsada,ganin mutane Bai Sa ta canja kaya ko ta saka Hijab ba haka tayi zamanta,aji take ja da kyar tace sannunku,barka da fitowa,Su Hajji suka zauna Haneef ko kulata baiyi ba ya haura sama,kin tashi tayi ta bishi sai da Hajji ya gaji yace ke wacce sakarai ce ne? Wacce shashasha ce ke ne? Mijinki guda ya fito daga prison amma ba farin ciki ba komai,Sai lokacin ta mike ta bishi sama,tana zuwa ta samu ya shiga wanka,zama tayi a gefen bed dinsa hadadden gaske tana ci gaba da chat dinta,tayi mugun Dadewa kafin ya fito daga wanka,Yana fitowa ya ganta me ya kawo ki nan? Ihsan tace Hajji yace nazo kasan in ba cewa aka yi nazo ba bazan zo ba,ka sani ba wai niyyar kaina bace abinci yana dining Kuma me dafa maka abinci ce tayi ba ni ba" tana fadar haka ta mike ta fice. Ita Ihsan tunda auren zumunci aka musu ba wai sonta yake ba itace ta damu da shi har aka yi bikin maimakon ta kwantar da Kai tayi biyayya baza tayi ba,tunaninta kullum shi Haneef sai ya gaji ya sakko da kansa ya kawo kansa da kansa,gadara take tana da kyau da komai da namiji zai so a jikinta sabo da haka ba sai tayi biyayya ba,itace mace itace take da aji,sai dai namiji yayi fadanci a wajenta ba ita ba,sannan tana ganin tana da babban aiki,babban matsayi ne da ita a company tana samun kudi sosai ba ruwanta da kudin namiji bata ga dalilin da sai tayi biyayya ba,shi yasa take abinda taga dama,yanzu ma company ne ya dawo da ita branch din Kano shi yasa aka ganta ta dawo gidan Haneef a nan amma ita a Adamawa take can gidan Haneef na can,sanda Wuta ta Kone Khairat ba karamar murna tayi ba a haka wai duk bata son kishiya Kuma,bata aikin fari bare na baki sai dai aikinta in tana gida Kuma chat ta fesa wanka ta zauna tayi Kallo,Bata fiye fada ba Kuma ita sabo da ajinta zai wahala kayi hayaniya da ita,tana da aji ita dole me aji ce,sai dai ta guma Maka takaici ta wuce. Tunda Haneef ya aure ta sun Kai Shekara kenan amma sau uku zuwa hudu ta taba kwana da shi,har wani Abu ya shiga tsakaninsu,tunda taga in Bata je ba bazai neme ta ba,sai idan taje wannan zai nemeta normal sai ta daina zuwa tace sai ya kawo kansa da kansa sabo da ta isa itace me aji ba shi ba. Shi Kuma Haneef Yana ganin abinda take yi haushinta ma yake Kara ji sabo da duk wani Abu na macen aure bata yinsa shi yasa baya kulata,ya Kai kararta sau biyu duk dangi ita Ihsan suke goyawa baya ai shi zai lallabata sabo da suna ganin auren zumunci ne ko ya Kai karar ba a daukan mataki shi yasa ya gaji ya watsar da zancen ya watsar da ita kowa yake Uzurinsa. Sai da ya shirya ya canja sutura me kyau cikin jallabiya fara me tsada dai dai shi sannan ya fito ya samu su Hajji su har sun ci abinci tafiya ma zasu yi,ya raka su suka shiga mota yace a fadawa Ummi ya bata zo ba Danta ya dawo,Hajji yayi murmushi yace zata zo ne a satin nan ko na sama tace,yace shike nan zan kirata a waya,in Kun isa lafiya ku kirani,yace to driver ya kaisu airport suka wuce shi Kuma Haneef ya dawo ciki,dining ya duba gaja gaja an lalata me aikin ya kwalawa kira Salamatu" fitowa tayi da sauri yace ki gyara dining sannan zan kawo wata me tayaki aiki,bana son Yan aiki barkatai zaki dinga gyara gidan nan ita zata dinga girki,Salamatu tace to Oga Allah ya kaimu, babbar mace ce ita Salamatu,yace me gadi fa ana bashi abinci? tace kullum sai ya koshi Oga,yace Good job yana murmushi yace zuba min ta zuba Masa ya dauki plate dinsa ya koma Palo Yana kallo yace Kai sai naga plasma din ta Kara min girma ko dan a can babu ne" ya Kalli gidansa yace Allah na gode Maka Ashe dai ba karamin hadadden gida nayi ba,sai yanzu na gano haka da naje prison,ga ac ta a can kuwa Ina wata Ac ta kirki,uhmmm ji Parlo komai me tsada ga kyau ahhh nasha wahala,shi yasa nake ganina kamar a Aljanna nake yanzu. Yau da wuri ma zan kwanta sabo da na hau katon bed Dina naji dadi in more rayuwa ta,da ace waccen Yar iskar mutuniyar arziki ce ai da sai ta zo ta Sha madarar Nido Inji Scola,tunda tafi so a bar mata abinta haka kullum a lullube taje da abinta ta Shekara tana rufewa,Dan ta ni in taje wanka ma kar ta bude,ita kuwa Ihsan tana garden tana hutawarta Bata San me yake cewa ba. Sai magriba yaje masallaci ya dawo Yana Sallar Isha ya kwanta abinsa,tunda ya dawo sai da ya kwashe sati guda Yana hutawa sannan ya koma aiki,Yana ganin kiran Khadija kullum amma bai San number din ba,yayi busy da yawa sai da ya cika 10days da dawowa sannan ya daga kiran Khadija,Yana dagawa yaji muryarta bai San ita ce ba,sallama tayi kana magana da Khadija ta gidan yari,Yana Jin Muryar ya gane dariya yayi yace wacce Khadija fa? Khadija me fasa gini mana dalla wacce kake ba Madara ta Yar kafa wai meye haka Dan Allah ka gane ni ka dinga wahalar da shari'a ,murmushi ya saki yace ohh Yar aikin da zan dauka?Mero tace duk Inda talaka yake sai me kudi ya nuna Masa rashin Kara kiri kiri ba komai itace ei itace Yar aikin,kin shirya ne? Mero tace tun yaushe Kuma na shirya na ma fada a gida sun yarda. Har kin gama Shan kokon ya ishe ki da awarar taku,Mero tace na Sha mana Kuma na fika lafiya ba,yace to yaushe kika shirya? Nifa a shirye nake ko yanzu,yace to gobe da yamma ki shirya za a zo a dauke ki, Allah ya kaimu,ki bar wayarki a kunne kusa dake sabo da kwatacen gidanku,Mero tace sabo da rashin tabbas din karfen nasara bari na tura ma text ko da network yayi tsiyar kaga ai an San Inda nake,yace Alright Allah ya kaimu,badan yayi dariya ba sai Mero taji kamar bai San wace ce ba yanda yayi magana. Washe gari sai da yamma likis mota hadaddiya tayi parking a kofar gidan su Khadija,Khadija babu suturar arziki 'Yan tsumman da suke a gida nata ta zabo kala uku masu dama dama,wacce ta dawo da ita daga prison a jikinta shi ta wanke ta goge Leshi yellow and Golden ta saka a jikinta,Mayafi ma tana so ta danyi too match amma ba dama haka ta dauki Hijabinta blue na yadi Dan Madina ta saka abinta ta fito dauke da ledar kayanta,Jummai sai murna take yi tana addua Allah yasa Khadija kije a sa'a Allah yasa wannan yasa shine silar arzikin mu,Allah ya zuba mana sugar a bakinmu Khadija karki bari ya zube bamu lashe ba,Dan Allah kiyi aiki me kyau Banda shiririta,Khadija tace to Inna baki sa min albarka ba,Inna tace Allah ya miki Albarka,Allah ya Bada sa'a,Abbun su Khadija Yana kasuwa tace ki cewa Abbu na tafi,zan fada Masa,Munnir Yana jinsu Yana tabe baki yace mutum yayi sana'arsa a gida bai fi ba amma ka dauki Yarka ka kaita wata uwa duniya baka San Inda take ba Allah ya kiyaye kar a yiwa Yaya Khadija Cikin shege,Harararsa Jummai tayi,har mota ta raka Khadija ta dawo tana ta tsalle tana murna a mota aka zo daukan 'yata,'yata tayi goshi,Munnir tashi yayi ya bar gidan gaba daya. Khadija kuwa tana mota a baya daga ita sai driver ba Wanda ke kula wani,duk surutun Mero shuru tayi har suka je unguwar Mero sai kallon hadaddun gidaje take yi,suka Isa katafaren gidan Haneef, ta Saba ganin gidaje masu kyau a Abuja shi yasa kalle kallen nata yazo da sauki,gidan Haneef ya hadu karshe ga motocinsa nan iri iri,Driver ne yayi mata iso har Parlo,tana bayansa Yana gaba,a Palo suka samu Ihsan taci shadda sky tana zaune tana Shan fruits,Mero gabanta ya yanke ya Fadi ganin Ihsan Masha Allah da ita son kowa kin Wanda ya rasa,a ranta tace Nima da kyau na ai ba fina tayi ba,ko haske baza ta nuna min ba sai gogewa da hutu kawai,fili Kuma tace Hajiya muna ta sallama Baki amsa ba,babu kyau wlh kaji sallama ka share a Islamiyya an koya mana,tuni Driver ya juya,Ihsan ta Kalli Mero sama da kasa a wulakance tace ke kama kanki,kece Yar aikin da Haneef yace an samo? Mero tace aka samo? Kamar kifi a teku Wanda babu me shi aka dakko dai ko Aunty, Ihsan Ido ta zaro tace Kinga bana son magana ta kwalawa Salamatu kira,Salamatu ta fito tace ga Yar aiki an kawo ki nuna mata komai ki kaita dakinta Dan Allah kuje bana son damuwa. Salamatu ta ja Khadija bangaren masu aiki ta nuna mata daki da bed da mudubi harda sip dakin me kyau abinta ita kadai,Mero tace ko a gidan miji ka samu wannan ai soyayya sai ba za ayi ba,Salamatu tace ke dai bari Yar uwa kin ga sanda aka kawo ni gidan Nan Inda kisan Yar gudun hijira amma yanzu kalleni kamar takari a saudiyya,Mero tayi dariya tace ai Aunty sai ace ma kece uwar Ihsan din matar me gidan,Salamatu tace ke rabani da wannan ba mutunci ne da ita ba,Mero tace nima Ina da degree din nawa rashin mutuncin,nawa degree din na rashin mutunci dan Cotonou ne ma,Salamatu tace kar a Kore ki baiwar Allah yarinya kibi a sannu kina Yar aiki Ina ke Ina ja da masu gida,Khadija tace zauna ki zuba Ido Aunty Salamatu ni ba ruwana da matarsa Ihsan,shi fa zanwa aiki Kuma ma muna mutunci da shi Yana da kirki,Salamatu tayi murmushi tace ke akan ma'aikatansa bashi da wani sauki aiki kika zo aiki zaki yi Kuma zaki Gani zaki ce na fada miki. Abinci ta kawowa Khadija tace sunanki Khadija ko? daga gobe zaki fara girkinki a kitchen ni ya Maida ni gyaran gida,Mero tace Allah ya kaimu. Mero tana nan har dare Bata ga Haneef ya shugo ba,ta fito Palo ta samu Ihsan ta canja sabon wanka da key din mota a hannunta da alama fita zata yi,ko kallon Khadija Bata yi ba ta fice,Mero tace mu ai sai mutum ya bude baki ma yayi magana komai shariyarsa Ina nan dake sai Kinga na fara yiwa mijinki tausa tukun kina Nan,tana zaune a kasa tana maganganunta taji kamshi ya mamaye parlon dagowa tayi a hankali tsorata tayi sosai ganin mutum a gabanta,kirji ta dafe tace wlh na zaci aljani ne,kallonta Haneef yayi tace Ina yini,ya amsa da lfy Alhmdllh,kawai sai Taga ya shareta kamar Bai Santa ba ya zauna a kujera,Mero tace kai, Salamatu ta fadi gaskiya kuwa ba mutunci,wani film aka saka aka fara series ne American film suna ta kallo. Khadija tace wannan yarinyar bata da wayo,Haneef yace tana kallo an kwace abin magic din an tafi Kalli yanda take tafiya,Mero tace rabu da banza ai jaka ce naga alama,Star dinne ya hadu da yarinyar suka tsurawa juna Ido Mero tace ka dauki remote a hannu za a fara iskanci, da kaga irin wannan kallon sai iskanci a canja tasha in an gama sai mu dawo,Haneef yace a'a ba wani iskanci da za ayi,Baki suka hade waje daya suka fara kiss Mero tace la'ilahhhhhhhhh....murmushi Haneef yayi,Dan Allah ka canja mana tasha kana kallo ya danneta ni dai ba ruwana, La'ilahhhhhhhhh...zai cire mata breziyya,wayyo tonon asiri marakisiyyarta ya cire,Haneef yaki canjawa yace in ana canja tasha ba a gane film,Mero kanta ta Maida bayan kujera ta buya tace in an gama ka fada min. Ihsan ce ta dawo ta samu Haneef da Khadija suna kallo suna magana,yace tashi ki Gani tsafinta ya dawo,ta dago da kanta tace ya dawo kuwa wlh ana Raina mana hankali gaskiya,Ihsan ta Kalli Haneef ta Kalli Khadija abinda ta tsaya yi kenan tana kallon su ko kulata basu yi ba,yace gashi Nan Bos yazo,Mero tace to ita yarinyar Ina tsafin tayi maganinsa mana,Inama nice....kaiii kuturun Uba ta dirga kansa Kalli wohoho...ya masge ta ariiiii.... Tare suka Kalli season biyu sai gobe Kuma za aci gaba,Mero tace sai da ya dakko dadi,Haneef yace gobe kamar yanzu zasu ci gaba ai,Ihsan bakin ciki yasa ta ja tsaki ta wuce. Papa ne ya kira Arham ga Mima a gefe Yana ta aikin lallaba Arham akan Basma,yace Dan Allah Arham ka rufa min asiri ka aure ta,mene laifinta kyakyawa da ita komai dai dai wlh ba Wanda bazai so wannan ba,kayi hakuri a hankali zaka so ta,Arham yace ai ni nace a zabo min laifi nane na yarda ai zan aure ta din,Papa yaji dadi yace ko me kake so zan Maka,Arham yace ai kayi min komai Ina karatu ka bamu jari muna sana'a yanzu dai ni a biya min Umrah in ana so aga na kula ta,Papa yace Inshaallah za a biya Maka amma ka Dan kirata kuyi zance ku fahimci juna ita tasan Kai zata aura na mata bayani,Arham yace yanzu a gidan ma sai naje zance?,Mima tace ji min yaro fa ni wlh wannan yaro ko tafiya yayi bazan kirashi ba ko awaya Dan bazan yi kewarsa ba,Arham yace ni din Mima? Ae Kai din idan Shaheed ne ko junior duk zan neme su in basa kusa amma ban da Kai dama ka isheni ni gwara ma ayi ma auren,Arham yace shike nan Mima za a gani ai kince dai ko a waya baza ki kirani ba in bana gari? Tace ae haka nace yace to shike nan. Papa in naje zancen ma in banda wakar Dan maliyo maliyo me take yi,kana ji dai a gidan nan kullum sai tayi wakar Dan maliyo,ita kadai tafa tafa take yi,tafa tafa tafiyar nan da zamu tare aikinta kenan fa, Papa yace marainiya ce tausayinta nake ji Yar abokina ce a kauye tun muna yara, Allah yayi masa rasuwa tun tana Yar karama,uwarta tayi aure aka tafi da ita agolanci gidan wani,Arham yace au agola ce ma?,shike nan mijin agola ne ni,Papa yace Kai gidanku tashi ka tafi,Arham yace agola kuwa gaskiya ba sa'a,haba shi yasa kirjinta ba komai,Mima ta make shi,Papa yace kyale shi uwarka ma gata Nan haka aka daura mana aure da ita a gidana ta fara,Arham yayi dariya yace Dan dai Kaine papa amma da na Fadi wata magana sai dai da kunya amma da nace sai yayi maganar kamar me kunkuni yanda baza aji me yace ba ya furta Kai ka jawo shi kenan ya fito,ya mike tsam,Papa yace ai baza ku nutsu ba kunyi gado ya zanyi, Mima tace ban gane sunyi gado ba,me kake so kace kenan wajen wa suka gada? Papa yace a bar dai maganar kawai tone tone ba dadi. Basma kyakyawa ce fara doguwa tana da sura da diri me kyau wulakancin Arham ne kawai sabo da yaga Yar kauye ce bata saka kaya a muhallinsu,Yana fitowa yaci karo da Basma ta fito da gudun tsiya Arham ya kurawa kirjinta Ido yace ba abinda yake motsi kyam haka, Kai ai ya kamata naga suna rawa in akwai amma kyaf kamar nawa tana gudu kyam da su,Allah ya kaimu anjima ai zanje zance wlh sai na taba naji bazan yarda da wannan rufa rufar ba,ko Kuma in tana wanka na Gani da idona baza a kawo min Abu a dukunkune ba,Su Haly ya samu a parlo suna ta Masa dariya haka kawai,suka ce yanzu matarka ta fita da gudu,Spark ya gani a parlon shima a zaune da Naila,Spark yace dama ita ce Basma din? Arham yace oho,Naila tayi dariya tace ai ni Banga laifinta ba wlh kyakyawa da ita haka,ni kyan fuska akace muku Ina so,kyawun kirji da baya ba ruwana da fuskar mace ni zan iya danne fuskar da pillow ma,Spark yayi dariya yace wai yaron nan aure za a Maka,Arham yace ya ranka abinda ka kasa ni zanyi zaka gani 9mnths da Baby boy, Naila tayi dariya tace wato Yan gidan nan baku da Kara wlh akan Allah bai bamu ba, Basma ce ta shugo da gudu kanta a kasa sanye da riga doguwa ta material silk,zata wuce tace sannunku tayi gaba Arham ne ya rukota harda bata rai irin ba wasa yace ke zauna ki huta da guje gujen nan,ke kafarki bata gajiya ne? Kullum daga Waka sai gudu haka kika ga ana yi a garin nan? Basma ta sa yatsa a Baki,Arham yace ke tun yanzu ba abinda zan miki wannan romantic sign ne bazan taba komai ba cire yatsanki,Spark kansa ya Dora a kafadar Naila Yana dariya,Basma ta turo baki tace to ai ni tunda nazo ban fita gari ba ban San me ake yi a garinku ba,ana gudu ba ayi ana Waka ba ayi ni Ina zan sani tunda a gida nake,Arham yace shagwaba zaki min ke Yar nan baki tafasa ba zaki Kone,Allah ya kiyaye na Maka shagwaba ni Ina na iya shagwaba,ni sirrina ma baza a sani ba Allah ya kiyaye kayi kadan kadan kasan sirri na,Arham yace ke Nan har sirri ne dake? rufa min asiri na San sirrinki yanzu ni Ina a'a ba haka nake ba ni sanin sirrin ya mace ai sai an shiga daga ciki,Basma bata gane ba tace to ni bazan shiga ciki da Kai ba,Arham yace nima haka Hallareta tana cikin rufin asirinta ba gardiyar da zata ganta,Basma Ashe tana Jin yaren tasan Hallare da fillanci,tsalle tayi tana dariya wlh yasan sunanta idan ba wannan Dan iska bane Allah ya Kona ni Dan iska ne,kana birni kasan Sunan abarku,yeeee Dan iska za a aura min ta tafi da gudu tayi cikin daki tana neman Mima zata fada mata,Bata ga Mima ba ta fito ta fice,Arham ya ja tsaki yace ta zaci tsoron magana nake agaban Mima Hallare Dan na fada mene ko Naila tana ganin ta Spark,Spark yace uhm uhm wlh kasan halina zan sa a kulleka a guard room wlh,kowa yasan tana gani mene sai ka fada tana ganin abarta ai an sani,Shaheed Yana zaune a gefe Yana ta dariya yace au abarta ce to a yanke a bata mu gani,Mufee basa wajen sun tashi tuni tare da Naila,basu San me Arham suke ba. Mufee ce ta Kalli Naila tace Aunty Naila wai ni wannan da akace Dan gidan Sudan ne ya sunansa ne? Naila tace Haidar? Ae Dan Uwan Ikhram din Rafeeq fa,shine dai Haidar din,tace gaskiya ba karya mashaallah,ko dai kina ciki ne Mufee? Naila ta tambaya,Mufee tace uhm ni Ina zan so namiji Bai ce yana so na ba Allah ya kiyaye,Naila tace in yazo fa? In yazo ai Kinga mutum bazai ki mutum ba,dariya Naila tayi tace kyaji da shi. Basma ce ta shiga part din Papa a nutse tace Mima kizo,Baki nayi? A'a nice nake nemanki zo ki gani,Mima ta taso ta zaci wani muhimmin Abu ne,suka taho tiryan tiryan har parlo ta nuna Arham tace Mima ki yiwa danki fada Dan iska ne dazu Sunan abarsu ya fada da wani yaren Yana bahaushe har ya Kai ya San sunanta da wani yare,Mima tace me? Abarsu ta fitsari mana ya Fadi sunanta kiri kiri da wani yaren Fulani Kuma Bai San na sani ba Ina Jin yaren ,ai sai Dan iska ko? Spark Yana jinsu yace Mima kizo in ganki tafiya zanyi ni,Basma tace Kuma ma Yaya Spark yaji sanda ya fada duk suna dakin nan babu Wanda ya Masa fada cewar Basma,Mima tace dole ayi Masa fada gaskiya,Arham Yana zaune ko a jikinsa,Spark Mima yayiwa magana na yan mintuna a gefe ya fice ya tafi,Mima ta juya zata tafi Arham ya Kalli Basma yace Enduu,hannaye ta Dora a Kai tace ya Kuma iskanci ya kuma iskanci wlh ya Fadi Sunan nono Mima,Mima baki ta bige mata,Basma tace ba nonon saniya ya fada ba na mutum ya fada,tsaki Mima ta ja ta harari Arham ta fice tace ki bari Basma zanyi maganinsa,tace to ta juya ta shige bedroom tana cewa wlh Dan iskan Miji ne nawa ni wayyo ni Kam na boni. Jibson ne ya shugo dauke da ledar nama biyu ya fara mikawa uwarsa mahaifiya nata sannan ya shiga da nasu ciki,Hanan wacce tayi kiba ta Kara kyau ta Masa sannu da zuwa ta mika hannu zata karbi ledar yace a'a ba sai kin karba ba zan ma bude mana muci,Hanan tace uhm sabo da nama ne,bana son Zalama kullum Naman nan sai kin ci fa daga dawowa sai kice ledar ma sai kin karba ai abin zai miki yawa ga sannu da zuwa kin yi min Kuma ace Leda ma sai kin karba kina Amarya kyale na ajiye na karasa sauran aikin kin San Ina kaunarki,Hanan tasan duk kawo nama haka yake yi amma Kuma a banza kullum sai anci,sai Hanan tayi zuciya ya bude Naman kaza gasashiya yace to taho,Hanan tace na koshi,murmushi yayi ya kalleta yace Allah? Tace bana ci,yace na gode miki Allah ya saka da Alkhairi,yaci gaba da dumurmusar namansa,Hanan ta tuna da Mohsin shi me hankali da shi ba irin Jibson ba,takaici ya kamata ta auri shashashan miji...tashi tayi ta zauna ta fara cin kazar taga ba ruwansa shi. Abba kwance yake a Saman katifarsa a shago wani yazo siyan wake,Ya mike ya zauna yace yawwa da Allah jawo min daron waken can,me siyan kaya yace Kai sai kace mace marar lafiya,kullum sai kana zaune ko a kwance yanzu kwanon waken ma sai na jawo maka,Abba ya mike yace duk abinda za a sa mutum ya tashi sai an nemo shi,ya auna Masa ya tafi abinsa,Abinci aka Aiko Zarah ta kawo Masa,yace har an gama girkin ranar? tace ae" to kice nace Allah ya mata albarka da take gama girki da wuri,Zarah tace to ta tafi,tana zuwa tace Umma yace Allah ya miki Albarka da kike gama girki da wuri,Yar Inna tace Ameen,bude Abincin yayi yaga shinkafa da Miya harda nama ga couslow an hada a mazubi dabam,yace bari naci sai na tafi Sallah da karfi na,ya zuba a plate ya fara ci yaji yace Kai kayan miyar nan anyi dacen su,ko dai Yar Inna ce ko kayan miyar akwai sa hannun Daya a ciki wajen bada wannan dandano. Wayarsa ya jawo ya kira Yar Inna ta daga tace wani abin za a kawo Maka? Yace a'a girkin ne yayi dadi shine nace bari naji kayan a miyar ne ko kuwa a kece ko Naman Dabbar ne taji kiwo haka? Yar Inna tayi murmushi tace a nice,tsohon hannu wasa ne,Abba yace na yarda yau ni zan tsefe miki kitson nan sabo da kin gama dani da girkinki,tace idan yara sun tafi makaranta ba,yace ae ai suna tafiya zanzo na warware miki kitson tace to,yace Kuma saloon zamu je,Kubra tayi dariya tace tunda akwai kudi ai sai muje,yace ni da nake da Naila da Mohsin ga Hidaya itama ta taka Leda kina gani dai Yar tatsitsiya Hidaya har ta rikita mijinta Dan banza kullum sai ya kirani kullum a waya wai gaisuwa ai nasan Bata Allah bace Yar Hidaya ta aka samu ana ta kwalbe ta,dariya Kubra tayi tace Kai dai komai sai ka fada baza ka barshi a ranka ba,yace wlh bazan barshi a raina ya kashe ni ba,Yar Hidaya ta ce ya samu bagas,kullum Abba Ina Kwana Abba ina yini sai kace na gari bayan Yana Nan kullum sai yaga tsirara,ni ba mutuncinsa nake gani ba tunda nasan me yake yiwa 'yata,Umma tace Yar taka ai itama kasan me take yi ne,irin su Hidaya hmmm,shi ya koya mata cewar Abba fitsararre. Yara suna tafiya makaranta Abba ya dawo ya zauna ya hau Warwarewa Yar Inna kitso da cumb harda rufe gidan kar ayi musu zuwan titse,Yana gamawa yace mu tafi wajen Chinaza ta wanke miki,Yar Inna ta shirya ta sa mayafi Abba yace kinyi local da yawa kamar ba kece uwar Naila da Mohsin ba saka Abaya,Kubra tayi dariya ta canja Abaya baka da mayafi yace yanzu kika fito a matar manya,baza a zaci nine mijinki ba fa an ganni Dan firit sai Kuma aga nine, dole mutane suce na cuce su,na yiwa masu kudi bakin ciki gaskiya,dole masu mota su dinga Jin haushi na a layin nan,Kuma a banza aka bani ke sadaki dubu daya,gashi a iya jikinki na Mori billions ai ni naci riba,Yar Inna tace muje Dan Allah ni ga Baby dauke ta,Abba ya dauki yarsu karama suka fito,Gidan suka kulle. Beauty ce tayi parking da sabuwar motarta da babanta ya canja mata,ta fito da katon cikinta,Abba yace ya kamata ki daina fita yanzu,Beauty tace na gaji da Zama Abba,Ina zaku je ne? Abba yace Saloon zan kaita,Beauty ta boye dariyarta ita Kam birgeta suke yi,tace to gashi nazo Kuma,yace to akan kinzo sai mu fasa zuwa Inda muka yi niyya ga key ki jira mu,Umma tace ba Nisa Beauty kinji yanzu zamu dawo,tace to na kaiku a mota mana Nima daga Nan sai a wanke min gashin,Abba yace a'a mu a kafa zamu tafi muna hirar mu,Kuma baza a kwaiwaye mu ba,kije wani wajen ayi miki naki kalar,Ina wajen za ayiwa Yar Inna ni zan tsaya kallon na suruka ta ne,Beauty tayi dariya kamar me tace Abba in aka mata sai ku fita ku shiga mota idan aka yi min sai mu taho gida,Abba yace to mijinki ya sani ne? Tace ba matsala zai yafe ma,Yace haka ake so kinyi kokari gwara ki dinga juya shi,motar suka shiga,Yar Inna ta shiga gaba Abba yace sai dai ki dawo baya sai a barni a bayan mota kamar birin turawa. Kubra ta dawo baya Beauty ta ja mota suka tafi,Abba yace Allah ya bani kudi na siyawa Yar Inna mota itama ta dinga kaimu unguwa,Beauty tace Kai fa Abba,Ina ni ko Keke bazan iya tukawa ba ai sai nayi hatsari naje na daki trailer bani da wannan kokarin Yar Inna dai Jaruma ita ta tuka,suna hira suka je Abba yace Chinaza ayi mata me kyau har relaxer a sa mata, gashin nan nata a Maida min shi na turawa,Chinaza ita kanta dariya take,Yar Inna tace baza ayi min kitso ba? Yace a'a sai wani Jikon na gaji da shi,aka gyarawa Yar Inna gashi gyara na gaske kamar Amarya za a kaita gidan miji haka aka mata,Abba ya nuna donut a Jikin hoto yace shi za ayiwa Yar Inna,Chinaza tayi mata sosai gashi ya zuba kyau,suna zaune sunfi 1hr ana Abu daya sannan Beauty ta shugo Abba yace ni na gaji Ina jiranku a mota ya shiga mota,aka yiwa Beauty itama nata ana gamawa Abba ya dawo ya biya kudin duka, Beauty tace har zan biya ma,yace a'a an gode miki jeki da abinki,da a baya ne ai bazan biya miki ba ko Yar Innar tayi kadan na biya mata kudin saloon,ki tambayeta kiji taci wahala,ko man gyada bana siya,yanzu kuwa bani da matsala zan mata ko mene. Beauty tayi murmushi suka tafi. Suna mota Abba yace yau Yar Inna sai ta Sha Ice cream a garin nan, Kai mu a siyo mata,Beauty ta wuce wajen Ice cream da kayan makulashe,Abba ATM dinsa ya mikawa Yar Inna yace kuje ku siyo, Beauty da Yar Inna suka shiga abinsu suna Hira suka yo siyayyar kayan makulashe sosai kuwa har yara aka siyowa,Beauty ma ta siyo nata duk a cikin kudin Abba suka dawo mota,Yar Inna ta mika Masa ATM card dinsa tace gashi,ya karba kawai yace nasan an min tafka tafka da barnar kudi,Kubra tace to ba kudinmu bane kudinka ai nawa ne,yace uhm haka kuka iya da wayo. Gida suka koma suka baje kayan makulashe har Abba kowa Yana cin abinda ya Masa,har yara suka dawo suma suka karbi nasu,Beauty har dare tana gidan,Abba yace kinyi girki dai ko? Kinzo nan kin rashe ana ta cin kudina dake ya batun Dana an Masa girki ko? Beauty tace har can naje na Kai Masa abinci Kuma nayi wani ma ya sani,a gidan ne tunani nake yi ko zan sauka lafiya ko Kuma a'a,Abba yace ki sauka daga Ina? da Ina kika hau ? Dariya Beauty tayi tace Abba ko zan haihu nace,yace au lafiya zaki haihu Inshaallah,tace Allah yasa,yace Ameen,yace Naila ta nake wa kwadayin samun cikin nan gata da dangin Miji masu surutun tsiya,bari na kirata naji Yaya,Naila ya kira ta daga suka gaisa yace ya gidan tace Abba lafiya so nake na wani satin zanzo,yace yanzu Naila kina wannan gidan me kyau har marmarin fita unguwa kike? Ai idan da nine ke wlh ba Inda zan fita Ina gida kullum Ina Jin dadina,Naila tace Abba ni na gaji da shi ma makaranta fa zai sani,Abba yace Inye Ashe dai za a gaji Yar Inna a Ilimi,to Allah ya taimaka,yanzu watanki nawa da bari ne? Naila tace wata biyu da Yan kwanaki Abba,yace Kuma ba komai? Tace ba komai Abba banji komai ba ko ciwon Kai bana yi bare na sa rai,Abba yace to na kusa Kuma fara yi miki kuka Naila abin nan yayi yawa sai tausayinki ya sani kuka Kuma,Kuma mijin naki kalau yake? Naila tace kalau yake Abba lafiya lafiya muke komai,Abba da Yar tasa Naila ba kunya,yace to Allah ya kawo Ina ta Miki addua,jiya ma tsohuwarki bacci na hanata sai da muka yi sallar dare sabo da muyi muku addua,Naila tace na gode Abba amma na karaya da haihuwar nan,Abba ko wacce in aka yi aurenta sai ta samu ciki. Abba yace to ai lamarin Allah ne ba a Masa dole shi yake bayarwa,irin su Jauro Kuma suce me? Gwara ke kinyi bari Jauro ko Jinin Haila bayayi,Naila ta kwashe da dariya,Abba yace Allah da Jauro mace ne ko Jinin Haila bazai yi ba bare ma a sa rai zai haihu. Naila tayi dariya kamar me har suka gama waya,suna gama waya yace Beauty tashi ki tafi gida kar Dana ya dawo bakya nan,kije ki kular min da Dana,ga surukanki amma bakya kiyi da ita,Beauty tana dariya ta mike ta dauki Jakarta,tace Abba zan Kara cake din nan,Abba yace ajiye Yar Inna ce zata karya da shi da safe,Kubra tace na bar mata,Abba yace gobe ma rana ce Kubra,Beauty dai ta dauki cake tayi Sallama ta tafi,Abba yace kice Ina gaida me gidan. Spark ne ya dawo ya samu Nailansa tayi shuru tana tunani,a gefenta ya zauna tare da Dora kansa a kirjinta ya kwanta ya furta duk tunanin cikin ne? Nasan bazai wuce tunanin haihuwa ba,wai ni da kika damu kanki Naila na taba miki complain? Ni wlh ban damu da dole sai na haihu ba,idan Allah bai bawa mutum ba kashe kansa zaiyi,wani yaron ma da masifa ne in aka baka shi,Kuma ko Shekara bamu yi ba amma kinbi Kin damu kanki,damuwarki baza ta Baki ba ko ta hanaki,in ma zaki hakura ki karbi kaddara ki hakura,addua ce kawai taki na mene na damuwa,bana son wannan abin da kike yi,da Allah kike fushi ko da wa tunda shine bai baki ba,Naila tace nifa ba tunanin haihuwa nake ba,bana son karya fada min meke damunki to ko takalma kika samo latest a siya miki a huta tunda ke rayuwarki a takalmin sawa zata kare,dariya tayi tace Allah ba wannan bane kawai yau ne naji bana Jin dadi sai na dinga Jin kunci da haushin kowa,Spark yace ko period ne? tace a'a haka kawai sai naji kamar nayi kuka, Spark yace to yi kukan mana tunda gani ba sai na lallashe ki ba,gidan Rafeeq zaka kaini na Dade banje ba naje naga me ciki Ikhram,murmushi yayi yace dazu naji yace yau bazai bude gida ba Kwalbewa zai yini Yana yi na matsa Masa a Office kwana biyu baiyi komai ba Muje mu hanashi sakewa,dariya Naila tayi tace ku dai wlh kamar abokai,Spark yace Khalid yazo ma da matarsa suna gari yace zai je can muje kawai,tashi tayi suka shiga wanka tare, Spark duk yanda hankalinsa ya tashi a toilet ya so ya kwalbe Naila taki yarda yau,shi tunda ya aureta bai taba nema ta hanashi ba sai yau,sai ta dinga Wayancewa,kyaleta yayi Bai nuna ya damu ba tunda jiki da jini sai ya rabu da ita suka ci kwalliya suka fito zuwa gidan Rafeeq,itace ke driving dinsu suna ta hirar su ta masoya,yace an dai hanani Kwalbewa,Naila tayi murmushi tace sai mun dawo zan baka Bado karka damu,nasan halinka sai ka fara Jin Haushin mutane. Washe gari Mero ta shirya breakfast,tana tsaye a Palo tana jiran Ihsan ta fito sai ta ganta ta fito daga bedroom a kasa,Haneef ta gani ya sakko daga sama dakinsa,Mero tace a'a lafiya? Haneef yace da aka yi me? tace naga ka fito daga sama dakinka daban,itama ta fito daga kasa dakinta daban fada kuka yi?me ya hada ku kamata yayi ace Kuna Jone ana tashin ku da kyar,ta bude Ido tace Baby kace uhm uhm koma bacci ban gama Jin dumin jikinki ba,amma sai na ganku baram baram,Kai kayi gabas da Kai ita tayi arewa da nata kan,Kai da zanji kace I love you,tace I miss you,ta lumshe ido,kayi mata kallon kauna,ya haka ne bafa mu gane ba mu,Ihsan tace amma ke ban taba ganin Yar shishigi irinki ba,Ina ruwanki to,mata da miji kika sani ko dazu na sakko na shiga wannan dakin. Mero tace karya ne Aunty tun asuba Ina palon nan Banga motsin kowa ba,Haneef yace kowa dakinsa daban yake kwana Khadija bama hada shimfida,Mero ta bude Baki tace ka kyaleta? Wlh ka Mori sadakinka ko ka Kara aure hauka ake a garin Fir'auna ka taso wlh karka yarda,Haneef ya boye dariyarsa,Ihsan takaicin Khadija ya kamata tace ke na Kore ki daga aiki Yar iska marar mutunci marar tarbiyya Ina ruwanki da aurena,bana shiga harkar mutum amma ke wlh mun sa kafar wando Daya dake,Mero tace Oga ya dakko ni ba ke ba Kuma gyara nayi Allah ya Gani ko a Islamiyya Malam yace in kaga ana ba daidai ba in har kana da hali ka Hana to naga Ina da hali Kuma zan iya shi yasa,Allah ya bamu Ilimi mun nema Kuma mun samu dole mu Fadi gaskiya Mero ta furta kamar gidanta ne,Shi Haneef dadi yaji ta birge shi,dama Ihsan ta dame shi,dining suka zauna,Ihsan ta bude abubuwan sai ta toshe hanci tace wannan wanne irin soye soye ne,Haneef ya kalla yaga shi normal komai ya Masa ya zauna yace serve me,Mero tace ya Maka Kai? Yace yes yayi min,tace an gama ta fara zuba Masa. AsmaBaffa [2/20, 2:14 AM] AsmaBaffa: 🏫TANTIRIYA🏫 A GIDAN YARI BOOK 3 ~TAIMAKO~ 26-30 Official By AsmaBaffa SADAUKARWA NE GA AIDA MAMAN TASNIM PAGE NAKI NE Chuzahraumar *ZINARIYAR MACE⚡* *Wai shin 'yar'uwa menene matsalarki? zubewar nono, ko kuma rashin kwankwason juyawa a falo maigida ya shiririce ya manta da tibi da matan tictok, menene matsalarki ne? rashin ni'ima ko kuma mugun sanyin da ya yi miki katutu, shin rashin taushin fata ne ko kuma kuraje da tabbani, ko bala'in ramar da ta addabeki kuma babu rashin ci ba rashin sha a gidan auranki, gwaigwayewar gashi ce matsalarki ko kuma kaushi da faso na tafin kafa da bushewar fata, kina bukatar fatarki ta yi glowing kalarki ta fita kuraje su mutu, ko kuma kina bukatar azababbun turaruka da humra tare da turarukan wuta. Na san dai kuna da yawa matan da tumbi ya yi musu karan tsaye ina nufin ya katse muku hanzarin yi wa maigida gwalli da muskuce-muskuce a falo😃 Nesa fa ta zo kusa AL-KUTUBIYYA ISLAMIC MEDICINE sun tanadar muku da nau'in magungunan da suke magance kowace irin matsala da izinin Allah. Babban burinmu shine sha'ani na aure ya inganta a samu daidaito. Muna da.* Na gyaran nono. Na sanyi. Dilka tare da hadin sabulu. Duk Wani nau'in maganin mata. Humra turarukan wuta perfumes, original miski tahra 3in1, ciccibi budurwar kaza. Had'addun supplement irin wad'anda ba su da matsala. Maganin Sliming wato narka tumbi. Abubuwan da muke sayarwa suna da yawa, kuma babu asarar dukiya. Muna garin kano kuma muna tura kayanmu kowane gari fad'in Najeria da Nijar har ma da kasashemn ketare. Kai tsaye a tuntu'bemu ta lambobin wayarmu domin karin bayani. *08089965176* *07084653262* Ihsan Ido ta zaro tana mamaki yanda yake sakewa da Yar aikin da jiya tazo ma,farfesun ya fara dandawa,tunawa yayi da kazantar gidan su Mero masu tace gasara da Skirt,yace ya batun tsafta kuwa nan dai ba skirt Kuma ba koko bane ko? Mero kamar ta sani tace ai tunda naje aiki Abuja na goge bana biyewa babar mu yanzu ma kullum gyara nake mata Ina so na koya mata yanda ake lamarin duniya,Ihsan tace uwar taki? Ae mana iyaye ma a ilimince idan anga suna ba daidai ba ta siga me kyau da tausasawa zaka fahimtar dasu,akwai wata kissa ta Sahabi na manta,Ihsan tace ke Jahila kice baki sani ba me kika iya kazama,Haneef ne yayi magana ya isa,itace kazama ko ke? Wanda yake gyarawa da Wanda Yana zaune sai dai ya zuba Ido ciki waye kazami?,Ihsan tace Yar aiki ce fa karka manta Haneef,yace to ita ba mutum bace,cin fuska ne wannan ai,ke baki aikin fari bare na baki Kuma ki damu mutane, Ihsan fushi tayi ta mike ta bar wajen tana cewa bazan ci ba bana ci,Mero tace ikon Allah Innallaha ma'assabrin Aunty Ihsan,Aunty Ihsan tawalkaltu alallah bazan biye ki ba Ina da hakuri ni,Haneef ya kalleta yace sit,na'am me kace? Zauna nace muci,Ido ta zaro tace muci fa kace,Uhum muci mana nace" zubawa kanki,Serve your self,Mero tace kana da kirki gaskiya,yace girkin yayi dadi kwana nan zan Kara miki salary double,kinyi abinda banyi zato ba,yanda nace zan biya ki ba haka zan baki ba zan Kara miki,Mero ta Sosa Kai tace na gode tana ta Jin dadi tana murmushi Farin ciki ya kamata tace yanzu aka fara harkar girki Oga,tunda haka ne zaka ga Abinci iri iri dama na koya a Abuja zaka Sha dadin girkina iri iri,dariya yayi, tace Allah sai nazo na fara zuba Maka Egusi soup,da miyar waterleaf Alaji ya Sha wata tarwada an gama,mu muka iya sarrafa abinci,ni da kitchen yake a tafin hannuna,Kuma nice wacce nasan sirrin tukunya babba da karama,tukunyar kasa data karfe duk nasan kalar dandanon girkin su,Haneef yace yana murmushi to zauna kici,zama ta gyara ta fara ci,suna cin abincin su,Ihsan leken su take yi ta bedroom,tana ci Yana satar kallonta, Mero duk da a kauye take abubuwanta na birgewa take yi. Sai da ya gama ci ya kwashe wayoyinsa yace Office zan tafi,Kallon film dinmu fa? Maybe na dawo kafin lokacin idan Kuma ban dawo ba ki kalla Kya bani labari Mero tace to an gama a dawo lafiya Honorable mijin Ihsan Yar wanka sai dai babu mamora,wlh ka dinga morar ta shi yasa take ma gani gani,kamar zaman maguzawa,shi yasa aka ce me shi ya Kara aure sabo da irin haka,yanzu da kana da wata matar da yanzu Ihsan ta kawo kanta tana make ma Murya Darling Ina Kwana,amma yau ko gaishe ka banga tayi ba,haba ko Fir'auna sai da ya zabo mace ta gari Asiya ya aura bare Kai Musulmi,Haneef Yana dariya yace haka ne Khadija zaki tayani zabowa na Kara ni kaina naga Ina bukatar mace ta gari,Mero ta washe baki tace in kayi aure zaka Kara lafiya da nagarta da daraja a idon duniya,amma wannan Ihsan ni da ita ai daya muke,Nima da zaka siya min kayan daukan wanka wlh haka zan dinga cakarewa a gidan nan bamu da banbanci,to yanda nake kwana na tashi haka take kwana,Dan Allah Kai baka ga ta Raina ma hankali bama,ka kashe kudi ka biya sadaki ta zauna a gidanka,Kaci da ita ka shayar da ita ga sutura sannan baka amfanar komai Kuma,ai cikin biyu ayi daya kodai ta dinga karbar Ijakala ko Kuma ka dauki mataki,a kirata ayi maganar nan a gabanta. Ihsan dama tana labe tana ji tace to munafuka algunguma Ina jinki,Kuma wlh sai kin bar gidan Nan na Kore ki dole ne aikin wai,oh my God kina sani magana,Mero tace ai ba wani Abu aka ce ba fada za a miki ni bazai yuwu na dinga ganin ogana Yana da mata Kuma Yana kwana ya tashi shi kadai ba,kije ki dinga bashi hakkinsa salary na nake ji,ya samu nutsuwa yafi Jin dadin bamu akan lokaci,yau da fushi ya tashi a gidan Nan so kike watarana ya kore mu sabo da rashin samun nutsuwa,in kin San hakane me yasa kika aure shi ai sai ki barwa masu sonsa,kullum cikin fushin ubangiji kike,Ihsan tace ya neme ni ne naki zuwa,sai ya neme ki zaki je,ba hakkinsa bane a bashi mana kayansa,Baki Ihsan ta bude galala tana kallon Mero,tace are you normal?oh bagidajiya ce ke dole kiyi,Mero tace me zaki nuna min ai na fiki ko kina da Ilimin bakya aiki da shi ke,me zaki nuna min kina Kashi kina fitsari wanne kwambo zaki yi, ki bawa Oga hakkinsa kawai a samu salama,bazan bayar ba idan Jikin na ubanki ne kizo ki dauka ki bashi Mero tace Allah ya kiyaye ma Ubana Sani yayi irin jikinki ai babu lafiya Kuma namiji da jiki irin naki,ke yanzu Dan Allah bakya ganin asarar man shafawa kike da kayan kwalliya? Miji baya yabawa ba ruwansa Dake kema ba ruwanki da shi,ai wlh in nice ke ko Mai bazan shafa ba,ko dangwali yaba bazan shafa ba bare Mai me kamshi,to asara ce babu me yabawa,ni da ke ba banbanci,Haneef Yana jinsu Yana latsa waya suna ta fama,ya fice abinsa,Yana fita Ihsan ta zazzaro ido tace ke ko uwar data haife shi ko uwarsa Hafsatu bata Isa ta fada min magana ba ki shiga hankalinki,bana hayaniya bana shiga Uzurin wani bana so Kuma a shiga nawa,in kika ce zaki shiga gonata wlh iyayenki sai sun bar kauyen ku tsirara,ki kama kanki bana shiga safgar rayuwar wani,Yar aiki ce ke ki tsaya a matsayinki duk da shi Haneef ya daure miki gindi,Mero tace a'a karki Masa sharri ta Ina ya daure min yanzu ma fitsari zanyi abina. Ihsan ta tsaya tace ke...ke...ki shiga hankalinki wlh na fiki rashin mutunci,Mero tace nawa rashin mutuncin degree ne dan Cotonou,naki kuwa bazai wuce na nan Benue ba,ki bashi jiki ki huta,wlh indai Ina gidan nan sai ya latse ki ya taba kudinsa bazai yuwu ba a dinga ci da rabonsa,naga uban da zai sa ya tabani to,kanin ubanki ne shi Haneef din,Yar iska marar tarbiyya berar kauye. Mero kalamai ta tausasa da lallashi tace Aunty Ihsan....Auntyna...kiyi hakuri haka zaki hakura ko dukiyar fulanin naki basu da girma ki daina Jin kunya,wai zai ganki kiji kunya ko ai abin kunya ne a gansu ba girma ba haka bane,nooo inji Spark....aure ne sirrinku ne ba wani zai fadawa basu yi masa ba,Kinga ko mu sai dai muyi hasashe cewar ba wasu manya bane amma bamu da tabbas tunda a riga kawai muke ganinsu,Ihsan tace na shiga uku yau Allah ya tsinewa uwarki,Mero ko a jikinta tace Kinga ki nutsu hakuri zakiyi haka Aunty kina so kema fa,Haneef fa ga kyau ga kamshi yanzu wata macen in ta ganshi sai ta fara zaucewa amma ke ana nuna miki hanyar arziki kina runtse Ido, kije kici arzikin Hallare Aunty,ki tuno farko farko sanda kika Kai kanki ya kika ji? Ki koma ki sake karbowa wlh,Ihsan gani tayi Mero kawai bata da Kai ta ja tsaki ta juya tana cewa idan ma hada baki kuka yi shi yace kizo ki lallabani to ki koma ki fada Masa jikina ban bayarwa in Yana so ya kawo kansa,ta juya a ranta tana murna cewar lallai Haneef da Khadija suka hada baki sabo da taje ya kwanta da ita,wata dariya tayi tace wlh tukunna ma Haneef,wasa kake da mata sai ka gaji ka kawo kanka kana roko na. Salamatu tana gefe ta Dora hannaye a Kai tana tsoro da mamakin Mero,sai da Ihsan ta bar palon Mero ta dinga dariya kasa kasa tace ai wlh sai bakinki ya bude Ihsan,aikin banza baki san ni ba so nake ya kwanta dake ba kawai Dan na hanaki sukuni ne Kuma gashi na saki magana,sai na koya miki masifa a gidan nan, Kya fada mana aji,aji indai bana makaranta ba bane ai aikin banza ne,Salamatu tafiya tayi ta buya kar ma Mero tayi mata magana ace suna gulma. Haneef kuwa har yaje Office Yana tuna Khadija Yana ta dariya shi kadai Yana Jin dadi,yace gaskiya fa yarinyar take fada na Kara auren nan yafi kawai,dama Mamana tana fada min ko waye ya bani shawara indai na duba naga ta kirki ce kawai nayi aiki da ita,kullum Ina bukatar mace amma ba dama,gaskiya zan dauki shawarar Khadija wannan ai me kaunata ce,Allah sarki tana so na samu nutsuwa Kuma gashi madarar Nido fa ta taru,wannan Yar iskar kuwa ko bata da lafiya wa ya sani ma ko aljani ya aureta oho,ba komai bari na dawo gida. Mero tana kitchen ta dora abincin rana Ihsan ta shugo ta bangajeta ta wuce ta dauki lemo a fridge ta fita,tukunyar Mero ta sauke tace yau sai yamma zanyi girki kowa yaci nade da Mai yau kin jawo wa kanki,sai Haneef zai dawo nayi masa,ta kashe gas ta fito ta wuce dakinta da biscuits da Madara,taci ta koshi tayi Sallah ta kwanta ta dinga baccinta har da cire kaya daga ita sai vest da pant . Yunwa ce ta damu Ihsan taga abinci shuru shuru gashi so take taci ta fita ta Sha wanka cikin material me tsada,fitowa tayi kwas kwas tana kwalawa Khadija kira,tafi karfin ma ta kira sunanta sai dai Yar aiki...Yar aiki ....Salamatu ce ta fito da gudu tace dalla ba ke ba ta gasken Yar aiki nake nufi,tsaki ta ja ta wuce dakin Mero da kanta ta ganta tana bacci daga ita sai dan guntun wando da vest,mamaki Jikin Mero ya bata kyau haka kamar ba Yar aiki ba,duka ta dannawa mero a cinya,ta bude Ido da sauri,Ina abincin dan uwarki? Me kika dafa nace? Mero tace nade da Mai,tsaki Ihsan ta ja tace Allah ya taimakeki kinyi girkin,wlh da baki dafa ba da Kinga rashin Mutunci,Mero dariya ta kamata wai Ihsan bata San mene nade da Mai ba,yunwa ce nade da Mai bata sani ba ta zaci wani lafiyyen girki ne. Tana fita Mero ta sawa kofarta key ta koma baccinta,Kitchen Ihsan ta shiga taga tukunyar ba komai,ta buda flasks duk wayam,dining wayam,Salamatu ta kwalawa kira ta fito tana hammar yunwa,tace Ina abincin da tayi? Salamatu tace ban sani ba Hajiya,tace min ta dafa nade da mai cewar Ihsan,Salamatu ta shiga tafa hannaye tace Hajiya ai yunwa take nufi,ai in kika ji ance nade da Mai to ba komai naci yunwa ce,Ashar Ihsan ta dura ta koma dakin Mero taji kofar gam,key din mota ta dauka ta fita kawai ta wuce eatery lafiyayye taci acan,tana cin Abinci wani matashin mutum talaka,kana ganinsa kasan sai dai rufin asirin Allah amma kyakyawa ne Siriri bai ko kama kafar Haneef a kyau ba. zama yayi a gefen Ihsan Ganinta babu mayafin kirki bata Masa kama da matar aure ba,sannu yace mata tayi murmushi ta amsa tana cin abincinta,order yayi ta fruits salat kawai sabo da baida kudin cin abincin,kallonsa Ihsan tayi tace ya fruits kawai? Murmushi yayi yace ba komai shi nake so ma,tace a kawo Maka irin wannan rice din akwai dadi,yace bata dame ni ba ne,tace a'a Kaci mana zan sa a kawo sai na biya Maka,yace nace miki bani da kudi Hajjaju? tace nidai nace ka dandana Kaci,okay fine ya furta Yana murna a ransa yau yayi gam da katar,tasa aka kawo Masa yaci ya koshi abinsa. Yana gamawa ya mike yace thank you Hajiya ya fice da sauri,Bai tsaya ko Ina ba sai Dan gidan da yake rabawa dakinsa me dauke da toilet da dan gado irin na gwauraye. Murmushi Ihsan ta saki ta mike ta wuce cikin rantsatsiyar motarta. Spark suna zuwa gidan Rafeeq a can suka samu Khalid Yana zaune a Palo tare da Rafeeq da Ikhram,Rafeeq yace ya Lagos din? Spark ne ya zauna ya hakimce Naila ta zauna a gefensa suka gaisa da Khalid da su Rafeeq,Khalid yace Lagos tana can Ina Barack a daure Ina hutawa Allah yasa ma tare da matata nake,Rafeeq ya furta har yanzu bata sake haihuwa ba? Khalid yace akan me zata haihu yanzu ana zaune lafiya,Soja in kaga Bai nemi mata ba sai kiyayewar Allah,saura kadan rannan na afka,na tuna Dan bariki Misam yanda ya kasa dainawa sai na fasa na ja abata na Maida ta ciki,Ikhram da Naila sai da ya basu kunya amma su ko a jikinsu. Spark tunda kayi aure banji ance kayi tafiya ka bar kasar ba bare kaki fadawa mutane,da kuwa kawai sai dai aji baka kasar Kuma baza ka fadawa kowa ba,Spark yace da kenan bani da nauyin kowa Gwauro ne ni Amma yanzu ko zan tafi kafata kafar me daki,Rafeeq Yana zaune Yana Shan fruits,Ikhram tazo ta kawo musu kayan Sha da na ci,Spark yace Tantiriya ga fruits Nan,murmushi Naila tayi tace bana son sha ni yau bana son cin komai,Why? ya tambaya tace haka kawai bana so. Yau me kika ci kwata kwata? Daga fadar haka sai taji haushin Spark wai har taji haushi nan da nan mood dinta ya canja da kyar ta daure sabo da mutane bata ce ya dameta ba,Spark tunda ya kula da haka sai ya kama kansa,bai sake yi mata magana ba,suka ci gaba da hirarsu da su Rafeeq,Nan ma sai haushi anki kulata ta mike tana cewa mu tafi gida,Ikhram tace ke Naila kalau kike kuwa? Naila tace kalau nake tunda baza a kulani ba mene amfanin zuwana,nazo kin wani share ni ke da nazo wajenki,Ikhram tace yau naga ta kaina ni yanzu duk maganar da nake miki kina shareni banji haushi ba sai ke,Naila tace eh ai Kya ce haka mana yanzu bazan sake zuwa gidanki ba,Rafeeq Ido ya zaro yace wlh da kin kyauta min ni dama Kun isheni Allah raka taki gona,Khalid dariya yayi yace madam dai yau ba kalau take ba gaskiya Spark ba haka na Santa ba,Naila ta fice tayi waje,Spark bai ce komai ba bai tashi ba bare ya bita,horn yaji tana ta yi Masa yaki fita kawai suka ji ta fice da motar tayi tafiyarta,Rafeeq yace yau kaga ta kanka Spark,dariya Spark yayi yace rabu da ita taje na koma a taxi,Khalid yace sai na saukeka a gida,ka lallashe ta Dan uwarka maybe wani abin kayi mata,Spark yace ba abinda nayi mata ni. Naila gidan Misam ta wuce,tana zuwa tayi parking kofa ta kwankwasa,Chika ta bude kofar tace au Ashe kece shugo,Naila ta furta mu gaisa a nan wucewa zanyi fa na biyo bai ma sani ba,Chika tace bai sani ba? baki Naila ta tabe tace ai namiji ba dan goyo bane ke rabu da shi duk ya sire min ma, halin Maza ai sai su,Chika tace Spark din? Naila tace me aka yi aka yi shi dan Allah canja zance,Chika tace to da dalili ko fada kuka yi? Naila tace ko daya ni wlh da zai barni na tafi gida sai nayi wata ban dawo ba ya ishe ni,Chika tace tab shi kuwa Spark lallai ba karamin laifi yayi ba tunda Naila dai tace haka,Naila tace ai mu dai mata sai dai Allah ya saka mana abinda Maza suke mana,babu na gari duk sun kare,na gari sun kare yanzu. Chika ta rufe baki tace ai sai hakuri Naila dama watarana dole a saba,Naila tace hakurin da nake da bawan Allah Nan ya isa,badan Ina hakuri ba Chika da yanzu zuciyata ta buga,Ki Kara hakuri kinji,ya zanyi na hadu da kaddara,sai anjima ta juya ta tafi abinta,Misam Yana Palo Yana Jin komai. Mamaki ya kamashi yace ke Honey Anya Naila kalau take kuwa tun kwana uku da suka wuce na je gidan naga tana ta fushi,Abu kadan sai ta fara fushi ta fusata,Chika tace Ina zan sani laifin Spark ne gaskiya duk yanda aka yi,Naila haka kawai baza tayi haka ba da dalili,Spark ba abinda zai mata tab wannan yanda yake sonta kamar ransa me zai iya tsinanawa bare ya bata mata rai,Chika ta furta dan kawai dan uwanka ne shi yasa. Misam Spark ya kira a waya yace wai me kayiwa Naila ne? Kai a Ina kaga Naila din? Yanzu tazo nan ta tafi tace badan tana hakuri da Kai ba da yanzu zuciyarta ta buga,dariya Spark yayi yace kyaleta fada take nema ni Kuma baza tayi da ni ba,Misam yace dama me zaka iya Kai kam akan Naila ai tubabbe ne. Naila tana komawa gida tayi parking ta fito ta shiga bedroom dinta ta kwanta haka kawai ta fashe da kuka take ta faman kuka a kwance a haka Spark ya dawo ya same ta,mamaki ya kashe Spark,yace Allah ya kaimu gobe mu tafi asibiti Ina zan iya wannan abu haka,Ina ganin wannan abin ai sai na rame ai, tana jinsa tana ta kuka,a haka tayi Sallar Magriba da Isha,girkin ma taki yi sai take away ya musu ya dawo,da ya kawo ma da kyar ya lallashe ta taci,yace tashi mu tafi to mu kwanta,kafada ta makale tace naje ka taba ni bazan je ba,Spark Ido ya zaro ba shiri yace kamar wata Amarya,Au dattijuwa ce ni wato na tsufa kenan,kawai kace na tsufa,yace ba haka nake nufi ba,ni a nan zan kwana,yace to ai da nan da can duk daya,ni dai za a dameni ta furta,Wanka ta shiga ta fito tayi Shirin bacci har da saka wando tight dogo da riga t-shirt da bra da komai kar a taba ta,Spark ma Yana Shirin baccinsa ya kashe light bai kulata ba ya kwanta abinsa gwanin tausayi yau ba Kwalbewa,Ido ta bude tace haka muke bacci Kai baka iya kula da mace ba,Ina Shan wahalar aure nidai,kowacce da Mijinta lafiya ni banda ni,ta Hana Spark bacci sai korafi take Masa baya kula da ita,hakurin da nake a gidan nan shi yasa ake min wani abin,sabo da anga Ina hakuri bana cewa komai,Juyowa yayi yace taho to dan Allah idan baza ki bani komai ba ki rabu dani nayi bacci,Naila tace ai ba abin arziki kake shukawa ba ,shi yasa kasan me kake min duk zaluncin da kake min hmmm ba komai,rungume shi tayi ba riga a jikinsa,ta dinga shafa bayansa tana cewa bayan nan zaiyi dadin cizo,wlh kamar na cije ka,bayan nan naka da cizo ya dace gaba daya,ban taba kula ba sai yau,Spark tun Yana dariya marar sauti har ya saki abarsa,ci gaba tayi tana shafa bayansa tace da gani ma duk Wanda ya cijeka zai ji dadi,hakoranta ta saka na kasa tana Masa susa da su,tace dan dai zaka ji zafi ne da na gwada. Spark yace bari ki gani dai naga kamar Kinga na kyale ki yau shi yasa,kayan jikinta ya hau cirewa tana hanawa suna kokawa sosai Naila harda kuka da cizon da yakushi baza a taba ta ba,Spark Kuma yace wlh bazan biye Miki ba,da tirje tirje da masifa da kukanta a haka Spark ya kwalbe yau yaci wahala,duk ta yakushe shi,sabo da fada yau Bata gamsu ba shi ya gamsu ta dawo Kuma tace sai anci gaba,yace ba abinda zanyi na gaji duk kin yakushe ni kin ji min rauni,ai Kaine da naci Spark naci ne da Kai baka Jin magana sai da nace bana so,to Kuma yanzu me kike nema? Ai ni ban kawo ba yau sai yanzu nake so,Yace bazan yi ba,Hallare ta gaji baza ta iya komai ba,wlh sai tayi haba haba tace baza tayi ba ai sai a tsine mata tabi duniya,please Baby,to fada min me na miki kike kuka yau kina fada da mutane me aka miki? In kin fada min shike nan,Naila tace domin Jin dadin zuciyata nayi,yace shine kika je gidan Misam kika zazzageni ko? Ka yafe min haushi naji Kuma wlh ban zageka ba nace dai baka min adalci Kuma nima ban San me yasa na fada ba ai kana min kai,Misam shine ya fada Maka sabo da gulma. Komawa tayi jikinsa tana cewa please,Spark yace duniya sabuwa ni ai yanzu zan kwalbe kwantar da hankalinki ke da harijinki. Washe gari Spark Yana niyyar Kai Naila Asibiti sai ya ganta ta dawo normal kamar da sai ya share yace ai mood ne dama ana samun haka,sai da yaje Office ya dawo wurin magriba ya dawo ya sameta a turbine Kuma ba mutunci. Arham ne yayi wanka ya zuba kyau shadda yasa fara,ba karamin kyau yayi ba,ya fito Yana goge takalmi sai kamshi yake,Mima tace Ina zaka je? Yace birthday party,amma kasan abinda Papan ku yace ko baka Jin magana kenan,cewa yayi fa yau kaje kuyi zance ku fahimci juna da Basma Kuma na fada mata ta sani,wanne irin iskanci ne wannan, wani ne yasa kace a zabo Maka kana son aure,sabo da Kun Raina mutane ba a isa a fada muku kuji ba kenan,indai kana son ranka ya baci ka tafi birthday party,Arham yace a gida take fa gobe sai na nemeta,ai ba gobe yace da kai ba,ka sani Kuma,Arham hakura yayi yace shike nan kice mata tazo,'Yarka ce ni da zaka aikeni ta juya ta bar wajen,Arham yace kai sai kace wata yarinyar azo a Gani,su Mima an Mima yabi yace to a Ina zamu yi zancen? gidan ubanka sai na fada Maka,shuru yayi ya kira Mufee a waya yace Ina Basma take? tace gata Haly tana shafa mata powder, kice Ina jiranta a palon baki na sama,Mufee tace uhm Ashe zance za ayi bari muzo muga wankan,yace wlh ba ita nayi wa ba,party zanje Mima Kinga yanda take fada akan yarinyar nan,laifinka ne ai gata nan zuwa yace to ya kashe wayar ya koma palon da yace taje ya zauna Yana danna wayarsa. Fitowa tayi tana Jin kunya tana bin Jikin bango akan an mata kwalliya yau ta sa sabuwar doguwar riga ta atamfa Mima tayi mata dinkuna kala kala,Haly har dauri tayi mata,shine take Jin kunya bata saba ba. Bata taba yin zance ba sai yau,yanda kawayenta sukeyi ta tuna,daga ance zata yi zance shine sai kace yaje gidansu tazo tana kasa da Kai ta durkusa a gaban Arham tare da furta Ina yini,Arham yaga ta tsula kyau kamar ba ita ba,a ransa yace ashe fuskar ma abar yabawa ce ba iya gaba da baya ya dace a so ba,muryarta yaji tace Ina yini,Shima ta Yan kauyen yayi mata yace lafiya kalau kalau Alqur'an,tace an yini lafiya? Yace lafiya kalau,ya mutane gidan? Yace gaku an lafiya,tace ya....latseta yayi yace ke kin isheni da gaishe gaishe ban Saba ba,tun Ina biye Miki Ina miki Kara Abu Kuma sai Nisa yake,in kika ce Ina yini ko ka yini lafiya kawai kiyi shuru haka,tace to ai Ummati tace haka ba tarbiyya bane,yace ni a wajena tarbiyyar kenan,tace to bari na kawo Maka ruwa,Arham ya bude baki yace ni da gidanmu,ai wajena kazo,Kuma ance bakinka Annabinka yace to jeki,tashi tayi tana gyara mayafinta ta tafi taje ta dawo dauke da ruwan da lemo a faranti su Mufee suna ta boye dariyar su har leke suke yi. Tana kawowa ta ajiye Masa ta zuba Masa lemon a cup tace kasha Dan Allah,Arham a ransa yace ubana ya zuba abu a dinga rokona na Sha karfin hali,dauka yayi ya Sha,yace ke baza ki Sha ba? tace a'a an hanamu cin Abu a gaban saurayi ance ba tsari,Arham ya Sosa gashinsa yace na shiga uku zanga rayuwa a gidana. Yace to zauna,ta nemi kujera daban zata zauna yace a nan zaki zauna ya nuna gefensa,ta ja gefen gyalenta ta sa a baki tana wasa da shi tana Jin kunya tazo ta dan dora duwawun ta kadan a gefensa,ga kujerar 2seater yace zauna sosai,zama ta gyara,Arham a ransa yace to ni me zan ce mata ma ne,tambayar ta yayi tunda yaga ita daga Waka sai shiririta ta iya yace ya Dan maliyo maliyon naki? Murmushi ta saki tace ai acan muke yi da shallu da reriye reriye me gudu ya gudu marar gudu ya tsaya sai a buya,Arham yace hmmm sai me? Sai tirke wasa da marmari fita da hawaye Idan aka Kamaka yaro wlh duka zaka ci sai dai kaji tas tas an hada ma jini da majina,Arham yace nine yaron? da mene to Kai?,ni na taba zaton a duniya zan auri kamarka ma,ana ganinka ai an San saurin girma kayi girman birni ne da nawa zaka girmeni ma,ai tun farko da Papa ya nuna min Kai aka ce Kai zan aura tun daga lokacin gwiwa ta tayi Sanyi,da farko na zaci mijin wannan Naila dinne kaga shi shekarunsa dai dai Dani,amma sai wai aka sake cewa ba Misam bane ba Rafeeq duk sunyi aure nace Papa to suyi ta biyu dani mana,yace a'a ai Kaine tun a lokacin na rike baki nace Kaine aka ce Kaine wlh ba karamin mamaki nayi ba nace zan karba da hakuri,Arham yace 5-0 ,kin min 5-0 yafi karfin 1-0 wannan sai biyar da kan Jaki,nufinki mijin Naila ya fini kyau? Murmushi tayi tace ba kyau nake nufi ba ai kaima kyakyawa ne duk Kuna da kyau wlh Allah shekaru nake nufi,Kuma ma namiji Ina ruwansa da kyau,neman kyau a namiji ai sai dan Daudu tunda dai an min kyautar ka shike nan,Arham yace ke zaki aureni ko ni zan aure ki? Aka dai bani Sadakar ki,Basma tace wlh ba sadaka aka baka ni ba sai ka biya sadaki cab, Arham yace to ke yanzu kina so na? da kika ganni kinji kina so na? Basma tace to ni dai ban San gaskiya ba, bana ganewa Ina so bana so ni ban sani ba kawai nidai rayuwa ta nakeyi ko da Kai ko ba Kai yo zan rayu mana,babu batun in ba Kai sai rijiya wlh ba ruwana ko bakin pampo bazan tsaya ruwa ya Jikani akanka ba balle ta kaini ga fadawa rijiya guda akan ka wallahi Bada ni ba,Arham yace 20-0. Yace to yanzu idan aka daura aure gado daya zamu dinga kwana,baki ta bude tace ni ba Yar iska bace ko babata dakinta daban dakin mijinta daban,Arham yace ke banza sai dare ya tsala take miki wayo tana tafiya,ai arcewa suke cikin sanda,Basma ta tsura Masa Ido tace babata Yar iska ce kake so kace? Yace iskancin aure ba,da bata je ba za a haife ki ne,ke wai cikin kogon dutse kike rayuwa? A karkashin dutse kike? duk iskancin mutanen kauye na zancen banza da labarin aure baki san me ake yi ba,Basma tace na sani mana ai hauka na manna Maka Kaine baka gane ba,ka gwada min iya duniyanci,mu mene bamu sani ba,mun San komai,dariya yayi yace haba? yanzu naji sanyi to me akeyi? tace ai in anyi auren Kaine Jagora Shugaba sai ka koya min ka sani a layi sai nabi,Arham a ransa yace ashe Yar duniya ce a haka kamar sakarai,yace uhm Lissafa min me miji da mata suke yi in anyi aure? Kai ta daga sama ta rike yatsanta daya tace na daya girki,na biyu tsafta,kwalliya,gyara gida,tattausan lafazi,fari, kisisina,wankan tsarki shi yasa aka ce kar a fiye yin kitso sabo kullum sai anyi,Arham yace wa ya fada miki? Kawata ce Karima dan kaji in fada Maka da aurenta yaranta biyu tana fari da Ido tana fadawa Arham,tace uhm to Ina ji sai me? Yin wanka da ango ai Karima ma mijinta Yana cudata nidai ban dani wlh bazan iya ba ni Kam haka kawai ai sai Hawan jini na ya tashi,yace to Ina jinki,da bacci shike nan,yace bacci ma akeyi?to da Kai me zaka yi? In baka yi bacci ba me zaka yiwa wani ko gadina zaka dinga yi? Arham yaga dai Basma duk yanda ya Kai ga son iskancinsa sai ta dakko wata tashar tana ta faman raina Masa hankali,yace bacci nake ji,tun yanzu zaka tafi ko goma fa bata yi ba wlh sai na fadawa Papa nace minti biyar kayi,Arham shuru yayi ya fasa tafiya yasan sai ta iya fada ta hada Masa sharri. Shuru yayi Yana danna waya tace kunno mana,kanta ta leko ciki,Arham ya fisge mayafin ba zato ya cire ya rike yace a gida ma sai kin fito da mayafi a Nan kike guje guje a gaban mutane,Dan Allah ka bani mayafina wlh zan fadawa Mima...ta furta da shagwaba,hannu ta Kai tana ja Yana ja,ga kwaro nan ya shigar miki riga,wayyo ta wajen Ina tana tambaya tana tattaba wuyanta,kawo na cire miki gashi ta bayanki ya furta ba wasa,ta juya da sauri yaga jela gashinta doguwa har baya an tufke yace a ransa Ina ruwana da gashi ni ko mace tana da shi ko bata da shi indai zata gyara gashinta normal. Zip din ya zuge ta wani yi sakato za a cire mata kwaro,ita ba bra ta saka ba,anyi anyi ta saka tace ita yarinya ce baza ta saka ba,yaga bayan ba birki,hannaye biyu ya zura ta bayanta ya taba Boobs dinta,mamaki yayi yace Kai to Ina suke makalewa ba a gani,a'a'a Papa idonsa Yana gani,wlh yana gani tar,Ita Kuma shashar wai ka cire min? Yace a'a kokawa muke ta yi da shi,kar ya cijeni dan Allah ta furta,Ina wajen Ina nan garkuwarki in bari ya cijeki,Yana ta tabe mata Boobs,ji tayi kawai abu daya yake yi ta tuna da kirjinta ne fa,wayyo Ummati ta kwalle da kuka wani ya taba min,sai da kika ce kar na bari gashi naci amanarki,Arham ya toshe mata baki da hannu daya hannu dayan Kuma ya gyara mata zip din yace ke daga taimako,ka taimaki kanka dai wlh sai na fadawa Mima da Papa ka taba min nono bazan yafe ba,wlh idan dai na samu ciki Kaine ta fashe da kuka. Arham yace dan Allah karki fada kinji ki rufa min asiri? In rufa Maka asiri azo a Ganni Ina laulayi Ummati tace ciki ake samu,wayo aka yi miki sabo da karki yarda wani ya taba da Hallare ake ciki,Karki fadawa Papa,tsoro Arham yaji Papa ya Masa warning yace wlh indai ya sake taba wata mace sai ya Kore shi daga gidan sa,shi yasa yake rokonta karta fada masa,Miman dai ko kin fada Mata ba damuwa,au haka kace wato baka tsoron babarka,yace kawata ce Kuma uwata,kashewa muke mu rufe itace ma ta zugani,dariya Basma tayi tace Allah zaka shiga wuta kace ta zugaka ka taba min nono? So na take da yawa tace inyi komai ba komai duniya ce in Mori kuruciyata,ke in banda ma kece daga naji yanda suke ai ya halatta,naji na gani dan Tabesting dai,ke da zaki ce ungo Sha ma,Ido ta rufe da hannu tace sai kace saniya da danta Allah ya kiyaye ba ruwa a nawa,yace akwai,a'a babu wlh ko shekaranjiya da naje wanka na gwada tatsowa,zan kawo Koko a cika min,dariya tayi tace nidai kana ta koya min iskanci sai sirrina nake fada Maka,Arham yace Kinga da na zaci Baki da komai a kirji,mummunan fahimta kayi min amma Ina da shi,yace naji zahiri saura gani da Ido,ashe zaka dige,yace ba wani digewa kina bacci zanzo na gani in naga dama,ance nauyin bacci ne dake,in kayi hakuri ma zaka gani what are you eating na mouth Yana zuba,dariya Arham yayi yace Iyye turawa sai kwai tace hmm baka San Ina makaranta ba Ina yin candy Papa ya dakko ni Kuma Ina Jin Dan turancina,na iya karatu da rubutu,suna haka har 11pm ta kusa sannan Mima ta zaci ma sun gama ta leko ta gansu a manne ba space,komawa tayi ba tare da sun ganta ba ta kira shi a waya tace kun gama ne? Yace a'a sai anjima,Sha daya na dare ta kusa ka tafi ka kwanta mana ka kyale yarinya,yace kufa kuka ce mu fahimci juna ban gama fahimtar ba,ka tashi ka sallameta ka tafi karka yiwa yarinyar nan wani abu ban yarda da Kai ba,Arham yace to,ta kashe wayar tana cewa sai ya tabewa yarinyar nan kirji wlh yaran zamani bare Arham nasan hali,Bata San aikin gama ya gama ba,tashi yayi yace tafiya zanyi,Basma tace kamar karka tafi Allah muna hirar mu,yace Mima tace muyi bacci haka,tace to sai da safe,yace ba kiss? Da gudu ta arce ta fada dakin su Haly tace cewa yayi wai ba kiss,Mufee tace uhm tsokanarki yayi tace wlh Kai wannan yayan naku Dan iska ne in fada muku gaskiya. Allah yasa bata ce ya taba ta ba,Haly tace ya miki wani Abu ne? tace yace kar na fada Kuma rufin asiri Yana da dadi indai mutum yayi Abu to a rufa masa asiri kar a tozarta shi,Haly suka yi dariya suka tabbatar Arham ya Kai hannu,Mufee tace ke dai ki Fadi gaskiya tace ai ya wayar min da Kai yace ba ta nan ake samun ciki ba Kunga kuwa da sauki,suka ce ae da sauki suna dariya. Spark a ranar yaga bazai iya da sabon halin Naila ba ya dauke ta yace muje asibiti kawai ko kwakwalwarki ce a auna in ta kama rukiyya za ayi miki ayi miki,ki sani a gaba da fushi da neman fada ga kuka,karshe kice zan dace da cizo sai kace Yar secret society, vampire kike nema ki dawo,driving yake tana jinsa tace Allah lafiya nake yace a'a sai fa munje asibiti,suna zuwa lokacin likitar tasu bata duty da wata ta hada su a lokacin,Naila bata yi bayanin me take ji ba tace ita kalau take,Spark ne yayi bayanin komai,Likitar tace Anya ba ciki ne da ita ba,Spark yace ku taimakeni ku gano gaskiya na samu salama kullum hakora take kafa min zanyi dadin cizo,Likita tayi dariya ta kaisu wurin test aka yi mata na jini,Likita result Yana fitowa tace to ka huta ma Oga ciki ne da ita 2mnths,yanzu in tayi wani Abu ka daina damuwa,Spark yace ba laifin glove bane batir ne Kai Kuma Baby zaka zo duniya akwai zama ni da Kai,zamu yi zama naji dalilin tsanata da kayi,ba laifin zaune ba na tsaye kasa matata ta dinga zagin ubanka,tana cewa na sire mata,Kullum bana baccin kirki sai Mita,sai fada,Kwalbewa babu,ga son a cije ni,Naila murna ta hanata fushin ma ta daina fushi gaba daya sai farin ciki kawai ta rasa me zata yi,so take kawai su bar asibitin,abin nema ya samu Naila murna ta hanata magana. Jauro yau matarsa Amarya da Habiba uwar gida ya dakko suka taho gidan Hashimu zasu yini,Hashimu yana gida yasan da zuwansu an shirye su Jauro ana tsakiyar mata,Habiba na gefe Amarya na gefe,Abba ya kalle su yace tattabara sarkin aure,Jauro yace Kai in ka isa kayi mana mace daya ce kwal baza ka iya adalci ba,Kai ba adali bane,Abba yace Kai adalcin kake yi, karka bari na fadawa Habiba abinda kake cewa,Habiba tace nasan zai aikata,bayan sun zauna Abba yace da jiya kuka zo baza ku same mu ba na Kai Yar Inna Saloon,Jauro yace uhmm tsofai tsofai haka? Abba yace daga can muka wuce Shan ice cream kasan ta da son Sanyi,Nima Ina Sha sabo da bana ciwon baya,Jauro yace bana son wulakanci Kuma tunda nace Ina ciwon baya Abu yaki wucewa a wajenka wai shike nan bazan warke ba to?matan ne suka gaisa suka fara hirar su suma su Jauro hirarsu suke yi,Jauro harda kiran Habiba da kanwata tace na'am,Abba yace Habiba Anji kishiya an fara canja hali ana so ayi soyayya ba a iya ba Kuma,dariya suka yi. Haidar kuwa Abuja ya shirya yaje katsam gidan Mima ya wuce wai yazo gaisar da matar babansa ya bata hakuri ta koma gidan mijinta,a zahiri Kuma wajen Mufeeda yazo,yaci sa'a tana nan kuwa a gida yazo har Palo aka sauke shi,Haidar ya nutsu bayan duk sunzo an gaisa,ya Kalli Maman Rafeeq yace dama hakuri nazo baki Dan Allah kiyi hakuri da abinda Baba yayi miki,ki koma gidansa,Maman Rafeeq tace na gode wlh ka nuna min kauna ka nuna cewa Kai me Ilimi ne,Haidar a ransa yace karya nake ba wajen ki nazo ba, amma badan da dalili ba me zai kawo ni wani ki koma hannun Baba Ina ruwana da zaman ku,kin dade baki koma ba,a fili Kuma yace ayi hakuri Mama a karasa haka,tace wlh bazan iya ba ka daina bani hakuri ma,bai ga Mufeeda ba ya zauna Yana ta jayayya da Maman Rafeeq har Mufeeda ta shugo ta dawo daga biki,tayi mamakin ganinsa sosai,kallon juna suka tsaya yi,Maman Rafeeq tana cewa bazan koma ba gaskiya ka fada masa,Haidar tuni ya samu abinda ya kawo shi ya ma manta da zancen. Mero tana zaune tana kallo ta gama girkinta ta shiryawa Haneef a dining sai lokacin me gadi da Salamatu suka ci abinci,tayi wanka ta canja jemammun kayanta ta zauna a Palo tana kallon ci gaban film din jiya,sai da aka gama film din ya dawo gidan,tace sannu da zuwa bayan ta amsa Sallamarsa,yace tashi kije Jikin mota zaki ga driver kice ya baki kayan Nan,Mero taje ta karbo kaya Niki Niki a Ledoji,ta kawo Masa,tana shugowa yace naki ne,tace na gode na gode Allah ya Kara arziki,ta shige part dinsu da kayan tana murna,tana zuwa ta duba readymade ne dogayen riguna na material iri iri,sai Abaya gasu nan kala hudu,sai undies,da flat takalma kala uku masu kyau da mayafai,Harda kayan kwalliya,mayukan shafawa da sauran kayan bukata,Nan take Mero ta saka rigar material wata white and green tayi mugun kyau kuwa kamar Yar birni,mayafi ta yafa fari a kanta ta gyara sauran kayan sannan ta fito,tana fitowa Haneef ya bita da kallo,ta Sha kyau matuka fuskewa yayi Yana cin abincinsa,Ihsan ce ta shugo tsoro ya kamata ganin Khadija Cikin wannan tsaleliyar shiga tayi kyau sai a zaci matar gidan ce,Mero tace kayi wanka kuwa ka zauna cin abinci? Yace yunwa nake ji bazan iya ba sai na fara cin abinci,Ihsan ce ta fisgo Khadija ta juyo da ita,ta kalleta kawai ta kwasheta da Mari,a gidana zaki dinga yin shiga haka dan kija hankalin mijina,dan uwarki muje,uban waye ya siya miki kayan ta nufi dakin Mero taga kayan a take away Leda tasan Haneef ne ya siyo,fitowa tayi da su tayi waje compound ta zazzage su a kasa gaba daya ta dakko ashana,Haneef ne ya fito yace wlh indai kika kona kayan nan a bakin aurenki,Ashanar ta jefar ta ja tsaki tace dama karya kake Karuwarka ce anzo a cuce ni a matsayin Yar aiki,Mero tace in kinyi zuciya kije ki bashi hakkinsa,in Kuna bakya so mu zamu bashi,Ihsan tace Karuwa Allah ya tsine miki ta wuce dakinta. Tunani Ihsan ta fara tace idan banyi da gaske ba yarinyar naga Bata da hankali da gaske take lamarin nan,wata zuciyar tace amma Kya zubar da ajinki kije wajensa ai sai dai yazo ya rokeni sannan na je tsaki ta ja tare da kwanciya a Saman bed. AsmaBaffa [2/21, 8:05 PM] AsmaBaffa: 🏫TANTIRIYA🏫 A GIDAN YARI BOOK 3 ~TAIMAKO~ 31-35 Official By AsmaBaffa SADAUKARWA NE GA AIDA MAMAN TASNIM Page naki ne Oum Aariz Follow this link to join my WhatsApp group: https://chat.whatsapp.com/LAizQA6PofSLoFhQ7XeaQx Ina kuke masu burin suga sun kawata gadajensu da hadaddun bedsheets? Ko Kuma blankets kike nema? Masu aurar da yara ko kannai da ke kanki uwargida indai kitchen utensils kike bukata To kukanki yazo karshe.kuyi joining group din R&U exclusive kitchen and more Ku more wa idanun ku da kayan kitchen Yan yayi na gayu da zannuwan gado na kowanne kasa Zaki samu acikin farashi Mai sauki Kuma Maza Bata barku abaya ba idan Kuna bukatar a hada muku lefe nagani na fada na amarya Kona uwargida wato na fadar kishiya duk Zata hadamuku acikin kwanciyar hankali.idan ma akwatunan kawai kuke bukata duk inkuka tuntubi Rumaisa zaku ganewa idanuwanku Tana Kano state Kuma Tana tura Kaya kowanne state afadin nageria harma da kasashen da muke makwagtaka dasu Zaku iya tuntubarta ta wannan number 07034559202 Ihsan tana zaune tana sake sake,Haneef ya gama cin abinci kenan zai haura sama yaji Muryar Mamansa,Juyowa yayi yace Mamana ashe kina hanya,Hafsatu tace ae dama cewa nayi in nazo ka ganni,Ina sa ranar zuwa na kasa,Akwatin kayanta ya karba yace sannu da zuwa muje" ta bishi sama,daki ma yace Mama wanne kike so ko na bar miki nawa na canja wani,tana dingisa kafa sabo da tana dauke da ciwon kafa tace baka da dama Haneef Allah dai ya Maka Albarka,yace Ameen Mamana,Ina matar taka ne? tana daki bacci take maybe,tace to mashaallah suka shiga bedroom ya ajiye mata akwatinta,ya durkusa tare da gaida ta tana zaune gefen gado,yace wanka zaki fara yi mamana? a jirgi na taho yanzu nayi wanka bazan sake yi ba,yace to abinci fa? tace uhm ai ku girkinku na turawa ne ni nafi son na gargajiya da zan samu tuwon shinkafa miyar gyada taji Alayyahu da yakuwa ai da nayi farin ciki,yace sai ayi miki yanzu dama na kawo sabuwar me aiki,baki ganta ba Mama nutsatsiya,Mama tace dama a kasar nan yanzu akwai nutsatse? Jinake tsadar rayuwa tasa kowa nutsuwarsa ta gudu,babu sauran nutsatse a kasar Nan,Haneef Kai dai indai mutum a kasar nan yake kawai ayi sha'ani a rurruma a zauna da hakuri amma batun nutsatsu yanzu babu kowa a fusace yake rashin mutunci yake tatawa. Dariya Haneef yayi,tace ya matar taka ta gyara halin kuwa? Yanda kika sani ba abinda ya canja amma kisa Ido zaki gani da idonki,Mama tace Allah ya shirye ta,Haneef yace an bani shawara ma na Kara aure kawai,Mama tace bazan hanaka ba Allah dai ya tabbatar da Alkhairi amma ni bana son aure auren nan,yace Ameen,tashi mu koma Palon kasa ta mike tana cewa wayyo Allah kafar Nan dai har yanzu ana ta magani kamar ba ayi ko ya nayi tafiya sai na gaji,an hanaki cin Jan nama sai kifi sai kaza,wlh watarana Karya doka nake,kasa ta sakko suka zauna,Salamatu ta fito ta gaisheta ta koma kiran Khadija,a daki ta samu Khadija tana gyara kaya tace ki fito babar Oga tazo ku gaisa,Mero tace to jeki zanzo,tana tafiya Mero ta dakko zanin kodaddiyar tamfarta ta daura tare da canja riga t-shirt ta fito a Yar aikinta sak ta fito. Tunanin Haneef kar Mamansa ta ga Khadija da shiga me kyau idan Ihsan tayi korafi ko me tace yarda zata yi,farin ciki yayi ganin Khadija a shigarta ta Yan aiki,yace a ransa wannan tasan me take,Mero ta karaso ta durkusa da uban ladabi ya gaisar da Mama,ta amsa tace ke Kuma ya sunanki? Khadija Mero ta furta tana murmushi,daga wanne gari? Khadija ta Bada amsa tace mashaallah gaki kuwa da nutsuwa,Mero ta sake yin kasa da Kai,Sai ta birge Mama,tace na yaba da hankalinki gaskiya a kula da aiki sosai,Khadija tace to Inshaallah,yawwa tuwon shinkafa zaki mata miyar gyada da yakuwa cewar Haneef,tace ai ba yakuwa yanzu gashi dare yayi bare a siyo,to shike nan ki mata miyar gyadar da ganye kawai tace akwai Ugu sai ayi mata miyar gyadar,Mama ta furta a sa kifi banda Jan nama,to ba damuwa Mero ta mike ta nufi Kitchen,Ihsan ce ta fito Taga Mama,murmushi ta saki ta karaso tace sannu da zuwa Mama,Har gabanta tazo ta durkusa har kasa ta gaishe ta. Mama tace Kuna lafiya ko? Ihsan tace lafiya muke Mama,Haneef ya kalleta kawai suka hada Ido,Baki ya tabe ya dauke Kai,me zaki ci Mama na dafa miki? mama tace an sa Yar aiki ma,Ihsan tace haba Mama aikin me nake yi ni ban fiye son Yan aiki su min girki ba a gidan nan,Haneef mamakin karyar Ihsan ya kamashi,Mama a ranta tace wato Haneef karya yake min dan kawai basa shiri ne shine yace bata kula da shi ai gashi na Gani da idona. Mero tana kitchen tana girkinta,Haneef ya shugo kitchen din kamshinsa ta ji a bayanta ta kafadarta ya miko kansa tare da yi mata rada a kunne kina da hankali Khadija,kin gane Mama zata iya fahimtar wani abin idan Ihsan ta fada mata ko me zata yarda amma a haka Kinga shike nan. Juyowa Mero tayi tana murmushi gwiwoyin hannayenta Yana Sama kusa da gas da wuka a hannunta,Ido ya zuba mata sosai yana karewa surarta kallo,Mero ma shi take kallo,me kike yi? Ya tambaya,tace girkin Mama,uhmmm ko zaki koya min? me zai hana kawai ka kalla yanda ake yi,yace Alright tare da harde hannayensa a kirji Yana kallon Mero tana girki. Tunda ta fara aikin ita yake kallo ba yanda ake girkin ba,ita Kuma sai bayani take Masa,tace yanzu yanka min albasa mu gani,Yana can ya kura mata Ido tace ka yanka min Albasa nace me kake tunani? dawowa yayi hayyacinsa yace sorry me kika ce? ka yanka min Albasa zo na koya Maka,yace kin San a kayan aikin nan ma kyau kika yi,Khadija tace Dan Allah? Yace t-shirt din ta miki kyau,na gode ta furta tare da mika Masa wuka tace kaga yanda zaka yanka haka,kamar haka to fara,fara yi yayi a hankali Dan bai iya komai ba,Kayi kokari gaskiya kawo ka gani,ta rike hannayensa da wukar a hannunsa suna yankawa a haka,dariya yayi yace na iya daga yau wow,Ihsan ganin shuru yaki fitowa ta shugo kitchen din,a zabure fakat da sauri ya dauki wani cup ya basar ka rantse dama shi yazo dauka tuni ya matsa daga kusa da Khadija,agogonsa yake gyarawa ga cup a hannunsa,Mero Kuma tukunya ta bude itama tuni a zabure a tamanin itama ta fuske,har goshinta take sosawa sabo da babu gaskiya,Ihsan kamar ta gansu manne da juna amma sai Kuma taga kamar idonta ne ya mata gizo,kallon su ta hau yi sosai tana so ta fahimci wani Abu amma sai ji tayi Khadija tace Oga kawai ka bar naman nan yayi kaga bai dahu ba ka daina jira in yayi zan kawo maka,Kallon Khadija yayi lokacin ta dago Kai suka hada Ido"Ido daya ya kashe Mata tare da murmushi,labbanta ta tamke tana mannewa kar ma tayi murmushi. Ihsan anci da rabonta tana danna waya tana dagowa har sun gama ya fice abinsa,Mama ya samu tana kallon film,Ihsan kuwa Mero ta kalla tace munafuka yanzu wato Kinga uwarsa kin saka kayan aiki,Mero tace Daya muke bakya girki ko cokali bakya dauke wa kince bakya so Yan aiki suyi miki girki,me take so zaki dafa mata ni Kuma Kinga Ina da kayan gayu na canja nasa na aiki,wlh kina fadar Abu a kaina sai na tona miki asiri yau kiyi karyarki da kika Saba kawai Nima nayi tawa,Ihsan ta Kalli Khadija tace karfa mayya sarkin naci an Kore ki kinki tafiya,na tsane ki Yar Zina,Khadija tace oho miki Kuma. Khadija sai da ta gama miyarta gefe daya tana tuka tuwon danyar shinkafa,shugowa Haneef ya sake yi ya bude fridge ya dauki lemon gongoni,ya sake cewa kawo na gwada tukawa ya ajiye lemon a gefe,ta bashi tana murmushi Yana farawa yaji tafiya kamar mutum na tahowa sakin muciyar yayi ya dauki lemonsa ya juya baya a zuwan budewa yake,Ihsan ce ta sake biyo sawu ta ga me yake yi wai.Khadija bata kulata ba haka ta gama girkin ta kaiwa Mama,taci itama sai yabawa take yi sosai. Mero ta dawo ta gyara wajen bayan ta gama ci tace Mama kina bukatar tausa? Mama tace a'a Yar nan na gode kawai dai ga magani na shafa min a Kafafuna,Haneef Yana zaune Khadija tace Oga ga aikin Lada kazo ka samu Ina Maka fatan samun wannan ladan, tashi yayi ya karbi maganin,Mama sai murmushi take yi tace kaji yarinyar kirki me Ankarar da bawa hanyar samun lada,murmushi Khadija tayi,Wallahi kin birge ni Kuma duk Wanda ya aure ki yayi dace Khadija,Haneef da sauri ya tambaya yace Allah Mama? tace duk Wanda ya aure ta ya samu macen kirki,Ihsan tana gefe baki ta tabe ta dauke kai,Mero tace Mama na gode za a miki wani abu ne? tace a'a an gode jeki uzurinki yarinyar kirki,Mero ta shige dakinta ta dinga sheka dariya tana tsalle a Saman bed tana cewa na ninke Mama bata Yar iska bace ni,babu wani ta gari,wai nice nutsatsiya dama ba Tinkiya aka yanka min ranar suna na ba. Washe gari Arham kin fitowa yayi Sam kar Basma ta ganshi ta fada tace ya taba ta,Basma kuwa tunda ta tashi take zuba Ido ko zata ganshi ita hirar jiya tayi mata dadi kwana tayi tana tunawa,Mima ta tambaya a Palo tace Mima tana Sosa Kai,Mima tace ya aka yi? tace dama jiya ya manta abinsa zan bashi Kuma ban ganshi ba,Mima tace bai fita ba ai Yana nan zai fito ne,naje na Kai Masa? Mima tace a'a ki bari ya fito,tace to ta zauna,Maman Rafeeq tana zaune tace karki sake naga kafarki a part dinsu ba a zuwa wajen namiji ki dinga taka tsantsan,Papa ne ya shugo da alama fita zaiyi ya samu Maman Rafeeq suna yiwa Basma fada karta je part din Maza,Mima tace ki bari ya neme ki da kansa,yaran zamani sai addua kuwa,Basma tace ai kuwa sai dai kar a Kuma jiya zip ya bude min yace kwaro ne a ciki wlh ya taba min kirji na,Amma karki fada Masa yace kar na fada,Ran Papa ya baci yace yanzu auren da za ayi Masa bazai iya hakuri ba,Basma tace ba haka bane ba fa yace kar na fada Dan Allah kuyi hakuri na yafe Masa nidai,Papa ya fusata,Mima tace Dan Allah kayi hakuri,yace ba ruwanki a gabanki yarjejeniya muka yi da shi da sharadi idan ya sake sai ya bar gidan Nan yace ya yarda,Kuma yanzu ya Maida ni dan iska,Mima tace to yanzu in kace ya bar gidan Nan Ina zai je? Kuma wa zaka yiwa auren? Papa yace na fasa bashi ita sai ta auri Shaheed shi ya bar min gida. Mima ranta ya baci tace yanzu...dakatar da ita yayi yace shi yasa suka gagari kowa,ke baza a yiwa yaranki fada ba baza a hora su ba,ya isa in zauna inyi yarjejeniya da shi sannan ya sake gwadawa shi din banza,Ina Arham ya tambayi Haly da shigowarta kenan,Yana part din su,yace kira min shi maza,ai Arham Yana ji ance papa na kiransa yasan ba lafiya,Haly tace da alama Basma ta fada Masa,Salati Arham ya saki Wanda ke shiryawa wanka yayi dama,yace guard room zai sa a sani ko ya kaini Barack a gana min azaba,Haly tace wlh kayi ta kanka Kai kasan ba iya korarka zaiyi ba kasan kalar korar Barack za a kaika kayi sauri na bude ma kofa ta baya,Arham ya kwashi takalma a hannu Suka fice a hankali ta bude Masa kofar kitchen ta baya yabi ya fita,ta waccen gate din na baya ya bi ya bar gidan Yana fita Papa Yana kiran securities sojoji yana bada sanarwa a rufe gida kar a bari Arham ya fita. Suka kulle ko Ina suka hau zaga gida da bindigu,sama ko kasa an rasa Arham,Haly tace na duba ko Ina baya nan,karya kike papa yayi kanta da jibga,Basma ta mike ta gudu tana cewa nidai bakuwar ce kar a hada dani ta arce daki,Haly da kyar ta Sha a hannun Papa ta kulle kofa tana kuka,Mufee tace Allurar Papa ta motsa ta sojoji,Arham kuwa Spark ya kira ya fada Masa,Spark yace me kayi to? Yace Basma fa kawai na rungume,karya kake Arham wlh idan baka Fadi gaskiya ba bazan rufa Maka asiri ba duk Inda kake sai an Nemo ka,Arham yace to abin na taba,Kuma wlh ni kawai ji nayi akwai ko babu ba da iskanci nayi ba,shine ta fada,Spark yace tab yanzu karka je gidan abokai Dan za a bika kana Ina? yace gani a taxi? zo Office dina kayi sauri,Arham yace na tabowa kaina masifa nonon Basma ko Masifa,Yana zuwa" Office din Rafeeq Spark yakaishi ya sa key ta baya ya kulle su har Rafeeq a ciki,Rafeeq yace ni a bude ni na tafi gida, ni ba da iskanci ba a kulle da ni,Spark bai ko kula shi ba. Rafeeq ya Kalli Arham yace kwarto,Ka taba me tsada yau dubunka ta cika,Arham yayi dariya yace bana dana sani Kuma ban Jin na gama tabawa, samun lafiya a daura auren nan,an lasa min zuma,yace wai Shaheed zai bawa ita,wlh bani ba Shaheed matukar ya karbi auren nan mun raba gari,Dariya Rafeeq yayi yace daga taba abu,yace ba haka bane,ai cin fuska ne wannan a bani mace ace za a canja ai ba daidai bane,ni har naji ma Ina Jin haushin Shaheed din. Rafeeq ya Kalli Arham yace baka Jin magana Arham,muga hannun ya canja tunda an Sha Laushi,Arham dariya yayi yace Kai da ka kwana a gidan surukai wa yasan me kayi, a gidanmu kowa Yana da abin fada ba Wanda zaiwa wani gori tun daga kakanni manya har yaran,Rafeeq yace Allah? Kaka Zeenatu ma karuwanci tayi,ai ance shahararriyar Karuwa ce da,harda kasa kasa da Murya yace Shima Maleek din ai a can suka hadu a Bariki suka yi aure,Rafeeq ma yayi kasa da Murya yace Allah Kai? Allah da dadironta ne ya aure ta daga baya,ta nace masa ai ance Zeenatu tayi Zuma ta more,duk Wanda ya dandana sai ya koma ta tara abin duniya da Bariki,Misam ne dai da ya shiga shi haka ya fito ba uwar komai sai nasa da ya kashe,Ashar Rafeeq ya dura Masa yace Dan iska munafuki duk a Ina kaji labarin nan Kai? Suna dariya Arham yace zancen duniya Yana buya ne,Mamanka ma uwar goyonka ai ance tayi Uhum Uhum kadan,Wlh zan tona ma asiri Papa yazo ya tafi da kai. Papa kuwa yasa aka dinga neman Arham basu San Yana Office ba har gidan abokansa kaf sojoji sunje ba a ganshi ba,aka je gidan su Spark duk an bincika baya nan,Mima ranar fushi tayi da Papa ko kulashi bata yi ba. Sai dare Spark yazo ya bude su,Rafeeq ya fice yayi tafiyarsa gida,Arham suka tafi da Spark gidansa. Naila tana Palo tana dariya ganin an taho da Arham,Naila tace to Ina kayan sawar? Na mijinki zan saka,kaga dai ka jawowa kanka kana zamanka lafiya,Arham ya ce ya zanyi nazo a dan gidan Soja,yanzu in ba Soja ba wa zaiyi haka,to ya Basma din? Na San mata shegen baki kamar na tsuntsu,Allah ya kaimu ayi bikin sai na saita mata bakinta wlh,sai na ladaftar da ita Yar iskar yarinya,Naila tana ta dariya tace ga abinci can,yace ni zan iya cin wani abinci ne hmm ya mike ya shige bedroom. Wanka Spark ya fito Yana danna waya Naila ta shugo yace wai dollar ta sake tashi,Naila ta sheke da dariya tace ai dollar a kasar Nan Bata San Inda zata tsaya ba,anjima ta tashi anjima ta sauka,Naira Kuma tayi haka Naila ta lankwashe kafarta tana dingishi tace Baby kaga Yar Gurguwa to haka Naira ta koma,Dariya Spark yayi yace ta karye baras,kamar a kasar Nan aka kirkiri dollar,ya kamata dollar ta koma kasarta ta gado. In kina so Kiga murna sai kin hadu da mutane baka San halin da ake ciki ba?,kice me dollar ta karye ana washe baki ana baki labari,anjima kadan dollar done High,Kuma ko wanne farashin kaya ya karu,Yan kasuwa sun rasa hankalinsu basu San me suke ba,yanzu ka mika kudi bani kaza ance Dari uku kana komawa anjima za ace dollar ta tashi dari biyar,har yaushe ya siyar da kayan suka kare ya dakko wasu,Naila tace ni da nake so in na haihu a yanka min sa da raguna to dollar tana ta hauka ya kenan? Spark ya kalleta yace wannan yaron na cikinki wai shi zan yankawa sa? Tunda aka same shi yake bani wahala ai Yana zuwa zai ga tsiyar Uba,dariya Naila tayi tace amma fa nayi kokari har yanzu ban fadawa kowa Ina da ciki ba,Spark yace karki fada rabu da kowa in ya fito sa gani kar ayi Masa baki kambun baka ya kama shi a haifo shi Dolo,tunawa yayi da Sunan surukinsa ne,Naila tace cin mutunci,yace sorry ba haka nake nufi ba,zata fara fushin yace Dan Allah yi hakuri,yi hakuri yi hakuri,yanzu sai Naila ta fara fushi ba gaira ba dalili. Bayan wasu kwanaki Beauty an hada mata gidanta chas,an gama furniture ta zuba musu na gani na fada,gashi ta shiga watan hauhuwarta ma,suna Palo Mohsin ya rike Beauty tana motsa jiki irin na masu ciki yanda aka koyar da su a asibiti,Beauty ta rike kugu suna dariya tace wlh na gaji,riketa yayi tare da zaunar da ita tana yatsina tace Marata ciwo take,to ko haihuwar ce? Murmushi tayi tace Edd ma sai Nan da 25days zai cika,da saur.....mararta ta rike tare da dauke wuta duf Bata sake magana ba sai da aka dauki minti daya taji ciwon ya saki,Mohsin Yana kallonta yace ya dai? Ko a kira Umma mu tafi asibiti? Ai na daina ji ma na warke,okay haka nake so. Kafin ta rufe Ido ciwon ya dawo da karfinsa tace Kai muje asibiti gaskiya ciwon nan ba na sauki bane ban taba Jin irinsa ba,sakkowa tayi kasa ta rike mara,tashi yayi yace tsaya na duba ki idan haihuwa ce sai mu tafi asibiti,da kansa ya duba ta yace to nidai haihuwa na gani,wayar Umma ya kira ta daga,yace asibiti zamuje ki shirya zan biyo na tafi dake Beauty ce Bata da lafiya kamar dai haihuwa ce,Umma tace to,Bata fadawa Hashimu ba kar yace zai je,tana shiryawa ta barwa Zarah karamar Yar ita muka fito,a shago ta samu Abba tace zanje unguwa,ko tambayar Ina baiyi ba yace a dawo lafiya Allah ya tsare ki siyo min tsaraba,murmushi tayi ta wuce. A gefen titi Mohsin ya dauketa suka nufi asibiti,Beauty tana salati a hankali tana cewa Allah ka zama gata na,Allah ka dafa mini,Allah ka sa min hannu a lamari na,Allah ka dafa min....a haka suka Isa asibiti,Mohsin hankali a tashe ya manta ma Umma tana wajen,zai fito da ita a mota sai rungumeta yake Yana cewa I'm sorry ni na jawo ko? Umma ta tace Dan ubanka ka matsa ka bani waje,Beauty tace jeka kayi min addua kaji,bazan iya tafiya na barki ba,Umma tace Mohsin zan bar Maka matarka na tafi wanne irin iskanci ne wannan,Karki yi fushi Umma gwara dai Ina ganinsa cewar Beauty. Gado aka bata,sun dade tun yamma suke asibiti tana Shan wahala,Beauty sai da haihuwa tazo ma'aikata suna wajen suna cewa yi Nishi...push....Beauty Bata ganewa sosai a wannan halin amma Taga yara ne Yan mata mace daya ce babba,tace a karance kuka gani Shegu Yan iska shi yasa kuke cewa nayi Nishi Ina naga karfin Nishi yanzu ni,baku San aure ba bare haihuwa kuce na dinga nishi,kawai Kunga Abu a rubuce kuzo ku dameni Nishin uwarku....tana Jin ciwo tana bala'i tace ban San me yasa Mohsin ya jawo wannan asibitin na Yan koyo ba,duk Yan koyo ne a ciki basu iya komai ba gashi Nan da wani asibitin ne da tuni na haihu,dama tunda aka sa Masa suna Aminu Kano teaching hospital,teaching ne fa na Yan koyo ake nufi ai bazan haihu da wuri ba,duk yara sun dameni ni,wayyoooo.....Ma'aikaciyar dattijuwa tace haihuwa tazo amma Kinga Yar iskar yarinya tana matse kafafu za fa ki kashe danki,Umma tace daina zaginta wahala ce ku har abada a kasar Nan bakwa girmama mutane,sai ku dauki mutum kamar wani Dabba,da iliminta wlh ta fiki Ilimi ma,kice ta gyara sai ki zage ta,Allah wadai da halinku wasu ma'aikatan lafiya marasa Imani mutum Yana wani hali Kuna zaginsa da hantara,sai lokacin likitar tayi shuru taji Umma ta fita masifa. Umma ce ta taimaka itama a nutse har aka samu Beauty ta haifo Danta namiji katon gaske, duk abinda ya dace anyi mata ita da jaririnta suka canja mata dakin hutu,Mohsin ana masallaci Yana ta addua Bai San ta haihu ba,har sai da Umma taga wajen 11pm sannan ta kira shi a waya tace ta dade da haihuwa fa Ina ka shiga, Alhmdllh ya furta yace tana lafiya? lafiyarta kalau gashi har Hidaya sunzo ma abinci take ci,fitowa yayi da sauri ya je dakin,a zaune ya samu Beauty tana cin faten doya Wanda Hidaya ta kawo,tare da Iman suka zo, Annoor ne ya kawo su, Mohsin sai murna ake taya shi baki yaki rufuwa an yiwa Amal kani,addua yayiwa Jaririn sannan yace an fadawa Naila? Umma tace Naila ka iya tunawa kawai? Murmushi yayi yace itace besty na,ban fada mata ba kuwa,Kiran Naila yayi yace kinyi da Your love ya haihu,murna ta fara tace me muka samu? yace me Hallare,dariya tayi tace Allah yasa ba Yar mitsil bace,ni ya gado ai,Kai Yaya ko kunya,Mohsin yace ke kika koya min ai, wa ya kaiki iskanci, kasa hakuri tayi tace zan fada Maka wani sirri karka fada tukun ciki ne dani ya kusa wata uku,Mohsin dariya yayi Jin Naila har rada rada ake fada,congrats kunyi kokari,Naila tace na gaske ma idan ban samu ciki ba kamata yayi a kama Spark ayi yamma da shu'umi kawai,dariya Mohsin yake sosai yace baza ki nutsu ba Naila,Naila tace to magana ta Allah baya hutawa da Kwalbewa Yaya ai idan ban samu ciki ba kawai ayi can da shi Inda ake cin mushe,Naila tana gama wayar ta juyo taga Sparka a bayanta wayar ta Maida kunnenta tace ai Dan Albarka ne ayi gabas da shi,Allah dai ya Masa Albarka Ina sonsa wlh,mijina ai duk duniya bani da kamarsa. Dariya Spark yayi yace ba laifinki bane Dana nane yake min zai zo duniya ne Allah ya kaimu,zanga me biya Masa school fees,Arham ne ya fito har yau yana gidan Spark Papa yaki hakura an kwashe kwanaki. Naila tace gobe su Basma zasu zo gidan Nan inji Mima,Arham yace Allah ya kawo su ni Ina ruwana da ita,Spark yace tana sonka fa wlh yarinya Mima tace tunda aka Kore ka ta kasa sukuni kullum sai taje Wajen Papa tana cewa ta yafe Maka a dawo da Kai,rannan ma kayanta ta hada tace zata tafi tunda dai ance Shaheed za a bata,Arham yace ita taga duhu wa yace ta tona min asiri,duk abinda za ayi da Yar kauye sai ta nuna hali yanzu da Yar birni ce waye ma zaiji kullum sai na taba kuji shuru Kuma kamar na biya sadaki amma dake ita ba a abin arziki da ita sai kuka wayyo ya taba min Dan iska sai na fada Naila tace a Yan kauyen ma taka ce haka Arham mu ba muka yi ba,Spark ne ya dingure mata Kai yace ka fadi Alkhairi ko kayi shuru,wannan cikin harda tone tone yazo,Arham yace au har anyi sabon? Naila tace tsokanata yake,Arham yace ni Ina ruwana ko cikin ne ma,Spark yace ciki ne da ita Arham almost 3mnths duk fushin nan da take yi da fada ai duk cikin laulayi take,Arham yace Allah ya raba lafiya,Spark yace Ameen wlh na matsu ta haihu na gaji da wannan mood din da take shiga,yanzu aka fara fa cewar Arham,kafin ta haihu nasan sai na dawo tsinke sabo da rama cewar Spark,dariya suka yi,Naila tace ya batun business din naku Arham? Shaheed ne yake ta aikin business din ai muna waya. Mima dai tace in Arham yayi tafiya baza ta damu ba ko kiranshi baza tayi ba amma kullum itace take fara kiransa,a rana sai ta kira shi yafi sau uku,yanzu ma kiransa tayi ya daga yace kika ce idan nayi tafiya ko nema na baza kiyi ba amma gashi yanzu kullum ke kike fara kirana,Mima tace ai ba wani missing Dinka nayi ba kawai dai Dan na tabbar da kana gidan Spark dinne kar ka tafi wani wajen,dariya yayi yace to na gode Ina Nan ai,ya fara hakura ai Basma tace zata bar gidan ta tafi baza ta hada Da da Uba fada ba,shine ya sakko yace ka dawo gida gobe,Arham yace ni nafi Jin dadin nan ma sai abinda naga dama a nan,to dai in ba so kake ka sake bata komai ba ka dawo gobe yace,Sai dai mu taho da Spark,to koma dai mene ta kashe wayar. Washe gari da wuri su Basma suka zo,Arham Yana bedroom abinsa Yana kwance Yana danna waya,Yana Jin surutun su,Basma taji ance yana nan amma bata ganshi ba,gajiya tayi tace Aunty Ina Arham din? Naila tace Yana bedroom waccen room din,Basma ta mike taje ta kwankwasa yace come in,ta tura kofar ta shiga,Ido ta zaro tace bleaching kayi? Naga ka sake haske,wlh saurin girma ne da Kai kwana nawa da barin gida amma har ka Kara girma,Arham yace me zaki ce dani kin Sa an Kore ni daga gidanmu,a gefen bed din ta zauna tace ban zaci haka ba ganin Kuna abinda kuka ga dama na zaci baza a Maka komai ba shi yasa,amma ai gaskiya tana da zaki Kuma tana da daci ko baka yi ba? Baza ma ki bani hakuri ba? Da kayan sata ka kamani da zan baka hakuri,nifa mijin Naila shine dai dai ni dai dai shekaru na ba Kai ba Dan ma ka samu Ina kula ka,alfarma nake Maka fa,Arham yace na gode zaki San kina min alfarma, dariya tayi tace hmm ta mike tace na tafi,tashi yayi ya mike ta ganshi da tsayi tace kana zuba saurin girma a duniya,kullum sai ka Kara tsayi,ki bari sai an daura aure ki fada min haka. Fitowa suka yi Yace kar a zargeni tunda ni yanzu na zama abin zargi a wajen mutane akan nono,abinda ma kowacce tashi tayi taga ya fito ba roka tayi ba Taga an bata shike nan sai a damu mutum sabo da anga mu bamu da shi sai mata su dinga wulakanta mu. Sai dare su Basma suka tafi tare da Spark da Arham,Arham sai buya yake a bayan Spark Yana cewa Papa ko bai hakura ba wa ya sani wlh Allurarsa ta motsa,part din Papa suka shiga matan suka wuce bangarensu,Papa Yana Palo shi da Mima suka shugo,Arham yace Ina yini barka da dare,Papa yace zo nan Arham,Arham ya ja da baya yaki zuwa,Kazo nace rigar Spark ya rike,Spark yace baza ka sake ni ba,Dan Allah Papa kayi hakuri wlh bazan sake tabawa kowa ba nayi alkawari,dama wannan ma sharrin shedan ne ji nayi an ja hannuna ban San dalili ba,bana cikin hankalina nidai kawai sai Jin Abu nayi a hannuna ban San komai ba,please Papa dama ni shedan ya dade da yi min fitsari a ka,amma yanzu zan dage da Azkhar na Kore shi,Papa mikewa yayi yace zaka ga shedan ya Maka fitsari a ka,Arham ya rike Spark zai gudu,Papa yace ai ba abinda zan Maka ni,da zan Maka da tuni nayi tunda nasan gidan da kake kyaleta kawai nayi,ruwa ya dauka ya zauna,Spark ya fisge rigarsa ya zauna,Yana cewa Papa kayi hakuri mana haka ya tuba bazai sake ba cewar Spark,Arham yace wallahi tallahi in sake tabawa sai na halak,baza kayi shuru ba kenan? Mima ta furta,shuru yayi ya zauna a gaban Papa Yana bashi hakuri,Papa yace ai na daina yi Maka fada Arham na gaji,Arham yace a'a Wanda ya rasa mafadi ya shiga uku ai sai na tabe,Kaci gaba da yi min na daina wlh,dama rashin hakuri nane amma Shekara biyu Ina Shan na uwata,Yaya Rafeeq ne ya zugani yace kar na bari kaina ya kulle Shima haka yayi,Misam ma Yana wajen lokacin yace Shi da yayi Bariki ma ya tuba ba abinda ya faru da shi bare ni,shine na kama zancen su suka kaini suka baro ni,to sarkin karya cewar Mima,tace haka fa ya fadawa Basma yarinyar da zata zama surukata yace wai ni na zuga shi ya aikata mata haka,Papa yaso yayi dariya ya boye yace ai Allah ya Kara tunda bakya son laifin su,Arham gobe yaushe? Yace Friday ka shirya gobe daurin aurenka,idan aka daura daga baya ayi bikin sai a Kai Maka Amaryar,Arham yace a bari Papa in aka gama shiryawa sai ayi bikin a Kai Amarya lokacin kaga maybe na fara sonta,baka sonta ka taba ta,Spark yace gaskiya a bari sai an gama shiri wannan sai a kaita tana laulayi,Arham yace a'a da kunyata ni ba ruwana da ita ni,Papa yace na gama shiri wlh gobe ana Sallah za a daura yanda nace haka za ayi tunda shi baya Jin magana. A daren Umma ta fadawa Abba cewar Beauty ta haihu,Abba yace amma kin ci amanata da baki fada min tun wuri ba, Kubra wlh watarana in kika yi min wani abin sai naji kamar na ambato kakanki Sarkin gandu Tanimu na zage shi,Yar Inna tace ai ka riga ka zage shi Kuma tunda ka Fadi Sunan,yace da Kuluwa me Kwan zabi,dariya Kubra tayi tace sai kazo ta kashe wayarta,duk kakannin Yar Inna ya ambata, minti kadan Abba yazo asibitin. Ya kalli Mohsin yace ya suruka ta lafiyar ta kuwa? Mohsin yace tana ciki zaka iya shiga,Abba yace o'o'o Yar Inna ce kadai zata shiga wannan dakin na gumurzu na iya shiga kowa ya ji da tasa tunda dai lafiya take shike nan in ta fito na ganta,ya kira Jauro yace kayi jika na biyu Jauro,Jauro yace Matar Dan namu ta haihu ne? ta haifi Da namiji,yace Allah ya raya tunda lafiya take ai anyi arziki,gobe zamu zo Inshaallah. Washe gari aka sallami Beauty fes da ita da Baby,direct gidan Umma aka kaita in tayi sati biyu sai ta koma gidanta. Abba yace wai nan aka kawota? wato mu a bata mana gida su Kuma su koma nasu gidan fes wannan ai wayo ne,kunci darajar babban bako me sunana,tun lokacin Abba ya bawa jariri suna Hasheem,ya kankane yace sunansa za a saka Masa,Mohsin yace dama ai sunan zan saka da mace ce Naila zan sa my love,Abba yace ai dama nasan sai ka mayar da sunanta itama haka Allah ya muku Albarka ya sake hada kanmu gaba daya,Mohsin yayi dariya yace harda Kai? Ku iyaye ai dole Kuna son mu ba matsalar komai mu yara mu za ace Allah ya hada kanmu,Abba yace harda ni mana idan na fandare fa na daina yi muku addua ai kaga gwara ace harda ni kanmu ya hadu,Mohsin yace to shike nan Ameen Yana dariya,Abba yace Azo a shiryawa Me jego farfesu suruka zata ci kudina a banza Nan da sati biyu tattalin arzikina Kuma ya kare ai,to kullum Yan barka zasu cika gida ayi ta girki ana saukewa ana dorawa,Allah ya taimake ku Abba ba irin na da bane Yan barka da Kun yini da yunwa a gidan Nan sai dai Kubra ta ci da ku ko Wanda aka haifar wa. Spark a waya ya kira Mohsin da Beauty ya kira su Umma ya musu barka,Abba ya kira Shima ya Masa barka. Kudin auren Rahma da Nabeela aka kawo sun fitar da mazajen Aure,Rahma Wanda suke rage zafi da shi suna Tabesting shine yaga gwara ya aure ta kawai bazai iya rabuwa da ita ba Sam,Shima Likita ne matashi bai fi mate din Annoor ba,Nabeela kuwa wani Wanda suke School tare ne da kadan ya girme ta sa'anta ne tare suka yi secondary har university,iyayensa suna da hali sosai shi yasa suka amince da yace zaiyi aure. Jauro sai murna yake zai rabu da wasu yaran nasa lafiya shi dai. Kwanan Beauty uku da haihuwa Nabeel ya sake kawo Hidaya da kansa,Abba Yana kofar gida shi da Jauro duk me zuwa barka a idon su take wucewa ta fito,Jauro yace gaskiya Dana ya iya kiwo har tana ta zama gwazarma,Abba yace uhm gata nan dai wlh tsila tana ta kauri,Hidaya tace Abba sannunku ta durkusa ta gaishe su,Abba yace wato Hidaya kasa zaki watsa min a Ido,kin nuna a gidana kafin ayi miki aure wahala kike Sha wato baki da kwanciyar hankali,gidan miji yafi gidan Uba,Anya in na mutu kuwa zaki yi kuka? sai da kika je gidan miji kika nuna kinfi Jin dadi acan,Ina rabaki da gorin da namiji yace a gidansa kika yi kiba,Jauro yace ai mu kowa ya shugo gidanmu sai ya canja. Nabeel ne ya karaso suka gaisa basu ce Masa komai ba anyi sa'a yau. Mohsin shopping mall ya shiga Yana yiwa me jego wasu siyayya da tace tana so,Hanan ce ta tsaya a kusa da shi da Mijinta Jibson suna siyayya,Jibson Yana cewa karki dauki abinda yafi karfina fa,a'a mayar da wannan wallahi ko kin dauka bazan biya ba,Hanan tayi murmushi tace to da uwar kudi na ni zan biya,Jibson Yana rike da hannunta,Mohsin ko kallon su baiyi ba Kuma yaji Muryar ya gane Hanan ce,Sai da zai bar wajen Yana Juyowa suka hada Ido da Mohsin,Hanan wai tunaninta zata cusawa Mohsin takaici ganin tayi kiba da kyau harda sake makalewa a Jikin Jibson ta furta my love muje,Mohsin tuni ma yayi gaba abinsa ko a gefen takalminsa. Yace a ransa dan kin auri me kwal kwal har wani birga zaki min ni da nake da me kayan arziki,aikin banza kin dameni a raina zan barki ki auri wani,ya biya kudi ya wuce da ledojinsa,Yana fita suma sun fito ya tsaya a Jikin tsaleliyar motarsa,Hanan ta saci kallonsa takaici ya kamata tace da tuni ni zan shiga motar Nan na cuci kaina,wai mene a kishiya da na zauna na dinga kishin hauka,gashi yanzu ni a Napep zamu koma gida mijina ko Lifan baida shi,kishin hauka baiyi ba na cuci kaina,anzo min da arziki na kasa hakura,matar tasa taso mu zauna lafiya amma naki" gashi yanzu ban samu ko Wanda ya kama kafarsa ba,Mohsin motarsa ya bude zai shiga ya juyo suka hada Ido da Hanan tana tafiya da Jibson zasu shiga napep Amma Mohsin take kallo,gwalo ya mata ya saki murmushi ya sake mata gwalo karo na biyu,da sauri ta dauke kanta kamar zata yi kuka,Mota ya shige ya ja sai ya Kara gaba sai dariya yake Yana driving yace kinyi asara Hanan yarinya yaro me kama da Nailan sa kyakyawa gashi yanzu gidana wow ga mota Alhmdllh,dama ni ba ajinki bane kuruciya ce ta sa na nace Ina sonki,sai da Abba yace ban iya zabe ba amma lokacin Ina yaro ban San ciwon kaina ba yanzu kuwa sai Beauty,wacce in ka kirata kace Beauty mutane zasu juya harrr kallon wace Beauty ana kallonta za a tabbatar da taci sunanta,ke kuwa da kika dace ma da suna Larai aka taimaka aka saka miki Hanan. Kidansa ya karo Yana bin wakar da yake ji har da rawa da kai yace Hanan kin mutu kin lalace an kare a me kwalkwal ko banza sanda kina matata ai kina shafa gashina,yanzu kuwa me zaki shafa kina kamowa zaki ji kamar kin shafa bayan kwarya,Mohsin sai dadi yake ji Hanan bata ci gaba ba, Yana Allah ya Kara, wannan dabiar Maza ce dama. Annoor Iman dinsa ya daga sama ya cafe ta tare da dorata Saman bayan motarsa ya tsaya a Jikin Kafafunta hannunsa daya a gefenta dayan ma haka suna karewa juna kallo suna Hira a cikin gidansu,ya dawo daga unguwa ta fito tarensa shine ya Dorata Saman bayan motar. Iman tana magana tana shagwaba kamar wata Yar yaye,tace Mamana tazo dazu wai kaji auren Sudan zata yi sun gama magana,yace mene na damuwa to yanzu ki gwada a kanki kice a ni da ke Hakan ta faru Dan na dawo baza ki aure ni ba? Iman tace da gudu ma ba wanda ya isa ya hanani wlh sai na aureka ba yara ba ko sabon gari market na Haifa dole na aureka,ai sai dai a sani a taskar labarai amma aurenka ya zama lahu,in aure abina in bar yaran suyi ta fushinsu,yace to ki kyaleta tayi aurenta duk abinda zai faru ya riga da ya faru,Haidar ya zama Yaya a gaske Kai jama'a Haidar surukina Dan iska ko gaishe shi bazan dinga yi ba,Iman tayi dariya tace Yayan guda,Juyawa yayi ta haye Bayansa suka wuce ciki abinsu. Kwanan Babar Haneef biyu ta tafi,tana tafiya a ranar Mero ta Sha wanka ta shirya cikin Abaya me kyau ta fito,Ihsan tana Palo Shima Haneef Yana Palo tazo ta wuce ta tsakiyar palon ta wuce kitchen,gaba daya hankalin Haneef ya koma kanta,Ihsan ta kalle shi tana mamaki,Mero tana sani ta wuce kitchen ta fito da ruwa Wanda ba Sha zata yi ba,ta fito again Haneef ya kura mata Ido Yana so ya fuske amma ya kasa,zata wuce yace Dan taimaka min da juice,Mero ta ajiye ruwan a gefe ta kalle shi suka hada Ido kasa tayi da kanta ta dago da iya idonta murmushi suka yi a tare,har ta tafi ta juyo tace juice kace ko? yace yes,wanne kalar tana kashe Masa Ido,Haneef yace dole na Kara aure ba waliyyi bane ni wlh,a fili yace Apple,tace haba me za ayi da wani Apple gaskiya ni na Strawberry zaka Sha yafi dadi,kasa musawa yayi sai me cewa yayi Allah? yafi dadi ko? Mero tace sosai ma,kamar nafi son Apple din ni,shagwaba ta fara Allah a'a ni gaskiya strawberry pleassssssssse kaji....tsigar jikinsa ce tace wani yarrrrrrrrr.....yace okay it's fine kawo min to shike nan? Kai ta daga a shagwabe,Ihsan mikewa tayi tsaye tace wai meke faruwa ne a gidan Nan? Mero tace da aka yi me fa? Yar aiki ce ni nazo miki da shawara kika ki ji,ai mu indai muka Bada shawara aka ki dauka to mutum sai yaga tsiya wlh,bama son mutum ma da ya yake karewa damu bare yayi mana,abinda kika kasa nake miki a aikace Kuma Baki ga komai ba,duk kudinki da kike ji da shi da iliminki ni ba ruwana da shi aiki zan miki wlh. Baiwar da Allah yayi mana ita ake fitowa da ita ana sarrafata tunda ke kin kasa kin wulakanta taki ta zama Bata da amfani,Ohhh kice dama son shi kike yi? ya halatta mana in ma Hakan ne ai ba haramun bane,wlh baza ki iya kishi Dani ba na tabbatar ko a kishiyarki nazo wlh sai kin sallami kanki,muke sa mutum yayi laifin dole fa,ki bar Raina mutun ko ya kika ganshi,ya kike so ayi miki? An fada miki gaskiya kinki ji,an miki fada an miki ta lallashi kinki to zama zaiyi yana jiranki ko me? bazai Mori kuruciyarsa ba jiranki zaiyi,so kike sai furfura ta fara feso Masa tukun,Yana da bukatar yara Yan dagwai dagwai,Haneef yace madalla da samun Yar aiki irinki wlh,ke Alkhairi ce,kina da hankali da hangen nesa. Ihsan tace haka ka ce? Dama Amana ta kuke ci ka kawo min Karuwa a matsayin Yar aiki wlh Iyayenka sai sun San wannan zancen,Mero ta juya ta dakko lemo ta kawo Masa,ya karba Ihsan ta ja tsaki ta juya tace fasikai wlh sai ka sakeni bazan zauna da mazinaci ba,Mero tace ai kinji Illar baki San ma waye mijin ki ba zai iya Zina ko bazai iya ba baki sani ba har kin fara zargi. Haneef tv ya canja channel yace sun fara film din nan,Mero tace ai Bata mutu ba? Bata mutu ba yarinyar to tunda bata mutu ba zanci gaba da kallo,Mero ta zauna suna Kallo abinsu,Ihsan ta shige daki tana kuka tana faman kiraye Kirayen kawayenta tana fada musu halin da take ciki. Haneef yace Khadija Aure fa zanyi na dauki shawararki, gaban Khadija ya Fadi dam,tace wace zaka Aura din? yace akwai wata Yar kawar Mamana ta Dade tana son na nine naki yarda Kuma har yanzu tana nema na a waya,Mero tace ba irinsu zaka nema ba ai sai ka Kuma auro irin Ihsan,yanzu karka nemi kowa addua zamu tashi a tsaye mu fara Allah ya kawo Maka ta gari to daga nan Kuma ko kawarka ce kaji baka so ku rabu sai ka aure ta,Haneef yace Kawa? Ni bani da Kawa sai ke kadai fa,Mero tace ko nice ba addua za ayi ba kan wacce ta fada ayi da ita,Nima ko ba na so zan taimakeka,harka ce ta taimako kana cikin wani hali,Haneef yayi dariya a ransa tunanin Mero zata iya Masa wayo,kawai kallonta yake,ta kwanta Masa a rai ne kawai,yace to shike nan Allah ya tabbatar da Alkhairi,tace Amin ni Yar taimako ce abokina nane Kai zan iya taimaka Maka a ko wanne irin lokaci,yace da gaske tace to in Kuma wata ce Allah dai ya baka ta gari ni bana bakin ciki,dama Ina da saurayina a kauye,Haneef yace wanne irin kauye ana zaune lafiya kina da aboki kamar ni. Ihsan ce ta fito a fusace ta haura sama ta shige bedroom din Haneef tayi Shirin bacci ta kwanta a Saman bed dinsa,Mero tunda taga ta hau sama tasan da dalili,dariya ta dinga yi a ranta tace tun ba a je ko Ina ba kenan. Haneef sai da ya shige dakinsa ya samu Ihsan a bed dinsa a kwance tayi mala mala cikin rigar baccinta me kyau. AsmaBaffa [2/23, 8:35 PM] AsmaBaffa: 🏫TANTIRIYA🏫 A GIDAN YARI BOOK 3 ~TAIMAKO~ 36-40 Official By AsmaBaffa SADAUKARWA NE GA AIDA MAMAN TASNIM PAGE NAKI NE ~aminaidriskafe Baiyi tunanin dakinsa ta shugo ba ya ganta a kwance haka,guntun tsaki yaja sannan ya kalleta yace fitar min a room,kin kulashi tayi,yace ba da ke nake magana ba,idonta ta bude a hankali tace na dawo ai,ka daina turo Yar aiki tana damuna dole sai na dawo kwana a dakinka,ka fada min ni da Kai ba wata Yar aiki ba,ka daina nuna min kana sonta dan wai nayi kishi,yanzu so kake nazo na dawo,ba matsala zan na kwana da Kai ka daina zancen sirrin mu da ita,tsaki Haneef ya ja yace baki da hankali amma naga alama,fitar min a daki,tsawa ya mata ta gaske ba arziki ta mike ta fara tafiya sum sum ta bar dakin yace stupid,ba aikin fari bare na baki iya sex ne aure an fada miki ya ja tsaki,Shirin bacci yayi Ya Kwanta tare da fara tunanin Khadija,yana tuna abubuwan ta Yana murmushi,Ihsan ce ta dawo ta sake haurawa Saman bed ta kwanta a gefensa,tashi yayi Yana masifa nace bana bukata dole ne,kin Raina min hankali ma,1yr da aurenmu tun farko Ina binki sabo da mu samu mu shirya mu zauna lafiya,ni ke kin sani Umarni nabi ba wai ni nace Ina sonki ba,amma duk da haka na danne na nemeki akan mu zauna lfy nan gaba zamu Iya fara son juna amma ke tunda aka yi aure ba wani Abu na kyautatawa da kika taba yi min. Prison naje baki taba zuwa ba ko sau daya,daga aikinki sai yawace yawace,sabo da kina da kudinki,wlh shi yasa Maza suke Hana mata aiki,suke karya su idan sun fara samun kudi sabo da wasu irinku mahaukata da baku San me kuke yi ba,kina tunanin son sex zai sa nazo Ina binki kina raina min hankali,sau uku kika taba biya min bukata Shima sabo da a lokacin na hanaki fita ne aiki shi yasa kika yaudare ni da shi,abinda yasa kika ga na saurare ki hakkinki ne yasa Ina tunanin kar Allah yayi fushi dani ,amma naga ke Yar rainin hankali ce,kin makara wlh,na baki dama kinki amfani da ita ni zan zauna Ina binki, da kudi na da komai ki kalle ni ki Kalli jikina Allah ya min baiwa Ina da kyau Alhmdllh,Ina da asali me kyau duk macen da na nema sai na samu . Baza ki godewa Allah ba Kin same ni bana neman mata,bana caca,bana Shan giya ko wani shaye shaye,ni ba Dan luwadi ba,duk irin wannan Allah ya kare ni bana ko daya,sannan auren zumunci ne amma ban taba wulakantaki ba ban taba fada miki wata magana mummuna ba,amma kin kaini bango wlh wlh bakya gabana yanzu ki sani bana sonki Kuma bazan so ki ba,kin sa min tsanarki a raina,Dan iska ne ni da zan zauna Ina zama da ke haka,dama na gane badan Allah kika aure ni ba akwai wata manufarki. Ihsan duk ta gama jinsa tace to ya zaka yi Dani ni dai Ina matarka zama daram,bazai wuce kace Yar aiki kake so ba Kuma na gani yanda zaka aure ta indai Ina gidan nan,Murmushi yayi yace idan so nake ko uwata baza ta sani ba za'a daura Kuma haka za a kyale ni,Jikin naki da kike wani ji da shi fin na Khadija yayi? Sannan wani dadi ne da ke? Skin din taki duk a cuccure a manne ya ja tsaki ya kwanta abinsa ya kyale Ihsan a tsaye sororo tana bakin cikin maganar da ya gaya mata,ta dade a tsaye kafin ta juya ta ja Kwafa tace wlh sai na nakasa Khadija naga tsiya sai na Maida ta gurguwa. Washe gari Khadija da safe tana kitchen tana girkinta,Salamatu tana gyara gidan,Ihsan ta fito da shirinta na tafiya wajen aiki,wankan da ta dauka ko matar da bata da aure baza tayi ba,riga da skert ta Sha na Leshi sun kama ta Sosai Dan mayafinta nata ziriri sharara,taci glass ba karya tayi kyau,Kitchen ta shugo tana uban kamshi,Khadija ta samu ta hankade ta wuce ta dauki Madara tace har abada bazan ci girkinki ba,Khadija tace kanki kika yiwa dama bake nake yiwa ba,ke wlh ki shiga hankalinki cewar Ihsan,Mero ta kalleta tace nufinki uwar gidana wai a haka zaki fita? yanzu ku uwayen gida Kuna haka Ina ga mu Amare,mu da zamuyi koyi a wajen ku sai Kuma kune kuke irin wannan,Haramun ne mace ta bayyana surarta da adonta ga Wanda ba mijinta ba,sannan wani yaji kamshinki ba mijinki ba kina cikin fushin Allah,wannan wlh gaskiya nake fada miki ki daina biyewa duniya kwana nawa akeyi a duniyar,sannan ba Wanda yasan lokacin mutuwarsa Ina jiye miki karki mutu a wannan hali Aunty, ki gyara tun wuri tun kafin a daura auren nan da ni,Ina zuwa kar na riga ki haihuwa Kinga ni yanzu a matse nake na girma da yawa irinmu ake kira da shiga da ragon ka,Ina zuwa zan samu ciki da ragona zan shugo,Ihsan tsaki ta ja tace an fada miki ni haihuwa nake so duk me haihuwa ta haihu ga waje nan,Mero tace to mun gode wlh zan kilo a gado,aikin banza wlh ba namijin da zai wulakantani akan wata da kudina da kyau na Maza matasa suna Nan a gari in dama taki sai a koma hagu,baka samu halak ba sai ka tafi wajen Haram. Mero tace Allah ya taimake ni Allah yasa bana Jin yaren da kike saukinta ma kenan ban San me kike fada ba,Dan Allah wanne yaren kasar kike? Ihsan ficewa tayi amma sai ta kasa tafiya ta zauna Palo tana jiran Taga Haneef me zasu yi da Khadija. Sakkowa yake daga step ya Sha shadda fara,kamar a sace shi yayi kyau Yana kamshi,agogonsa me tsada yake gyarawa,Khadija ta fito dauke da flask na ruwan zafi ta ganshi,Ido suka hada ya sakar mata murmushi itama haka" yace wai har kin tashi? Mero tace ba dole ba Oga bai fita na sallame shi ba Ina naga ta bacci,nifa a kan uzurinka idan ban kwana ba bacci ba Allah ya azurtani,idan ba cirrrr yanda naga dare haka zanga rana,Haneef harda shafa gashi yana Jin dadi,Mero tace kayi kyau Sir,yau mata zasu Kalli Allah ya isan Aunty Ihsan da yawa,dariya yayi ya nufi dining,Ihsan ta gama kulewa,to ita taki magana ta tsaya girman Kai. Mero bayan tayi serving dinsa ya fara ci tana zaune,itama ta zuba nata,Ihsan karfin halin Mero Yana bata mamaki mutum Yana da aure ga matarsa a gefe amma ki zauna Yana cin abinci kuci tare Kuma ga matar a gefe,Ihsan tace laifin Haneef ne da ace bai Bata dama ba ko kallon banza bata Isa ta min ba,wato shi yasa wasu suke kama miji a hannu,idan kina da miji a hannu to ba abinda baza kiyi ba Kuma ki zauna lafiya,shi yasa tunda Mero ta ciri tuta a wajensa shike nan sai abinda taga dama take yi a gidan ba dangin iya ba na baba. Muryar Khadija taji tace Ogana...ya amsa Yana kora tea,tace jiya kwana nayi Ina mafarkinka,dariya yayi ba shiri,yace me nayi a mafarkin? Khadija tace Ina bacci sai gaka kazo,nace Ina Kwana Hubby na,a mafarki fa nace Hubby na Kuma ka amsa wlh kace na'am Babyna,Haneef yace ni din? Mero tace tun yaushe Kuma,a daren jiya kaga yanda nayi wata hajijiya musamman batun da muka yi a daren jiya cikin mafarki,ai munyi batutuwa,Haneef Yana ta dariya yace Allah yasa banyi komai ba,kayi mana kawai dai ayi shuru da zancen nan ba na ji bane amma anyi batu,Haneef ya zauna Mero tana ta tsare shi da zance yaki tafiya wajen aiki har Ihsan takaici ya sa ta fita abinta. Tana fita tana so tayi parking wani me kurkura yazo ya daki bayan motarta kadan,parking yayi da niyyar bata hakuri ta fito itama a fusace tana masifa,wanne irin mahaukaci ne kai sai Taga Wanda ta siyawa abinci a resturanta kwana ki,tace Kaine? Yace oh Hajiya kece? Dan Allah kiyi hakuri akasi aka samu wlh,Murmushi tayi tace ba damuwa karka damu Jakarta ta bude tace wai ya sunanka ne? Sadeeq sunana,tace mashaallah ta mika Masa card dinta tace gashi ka neme ni,bani number dinka,ta tambaya tana murmushi,har ga Allah yayi zaton budurwa ce ya Bata number ta shigar ta kirashi yayi saving tata ya wuce abinsa itama ta shiga mota ta Kara gaba. Khadija kuwa da kyar Haneef ya yaki kansa ya fita daga gidan sabo da yanda yake Jin dadin hirar abin ba a magana. Sai yamma likis Ihsan ta dawo daga Office dauke da take away dinta baza ta ci abincin Mero ba ta daina ci, Clashing suka yi da Mero zata sakko daga sama itama Ihsan zata sakko,Mero tana gaba Ihsan ta sa hannaye biyu ta hankado Mero daga Saman bene,Mero ta saki Ihu ta gangaro ta fado taji munanan raunuka kuwa. Salamatu ce ta fito tana salati tayi kan Khadija wacce ke kuka kwance a kasa ranga ranga,tsaki Ihsan ta ja ta wuce dakinta ta saka key ta barsu a wajen tana cewa naga da shegiyar da zaka yi hira Haneef, Salamatu da gudu ta fita ta kira me gadi tace shugo Iro ka taimaka,Iro yace Aradu idan Aunty me mota ce bani zuwa sai dai ta mutu a kawo gawarta,ko sallatarta bazan yi ba bare naje kaita makabarta,Khadija ce ta fado daga bene,Iro yace Subhannallahi ita me ya kaita tunda ba sabawa tayi da hawa bene ba,ta Saba da dakinsu a kauye shiga kamota kamar dakin zomo,daga ka shiga ciki bugul ka fito,tazo nan birni ta saki jiki tace zata biyewa matattakala ai gashi nan,Habiba tace Aunty ce Me mota ta turo ta,Iro yace naji a zuciyata ,Hasashe na ya tabbata dama naji a raina itace sila,ai Khadija ce da shiga sharo ba shanu muje,Iro Yana zuwa ya dauki Mero yace nauyiiiiii....ya ajiyeta yace kut wannan ko mota ta shiga sai ta girgiza. Ya sake sa hannaye Khadija tana kuka ya dagata ya sake ajiyeta Yana Nishi yace me kike ci haka ke kuwa,ke daga wajen kasar Yumbu aka samar da ke,tabo me nauyi da danko da irin kasar aka samar dake,bazan iya ba ku Nemo wasu mazan,ya sake gwada daukan Mero sai ga Haneef ya shugo yaji kukanta ga Iro ya daga ta,Haneef yaji haushi tun daga nesa yake cewa Kai ajiyeta....sauke ta....Yana hararar Iro ya karaso wajen,in banda kai dan Iska ne Ina ruwanka da ita? Uban waye yace ka taba mata jiki? Iro yace Salamatu ce tace na taimaka Kuma ma Allah ya so sau hudu na gwada daukanta Ina ajiyewa Ina dauka nauyinta ya baci sai kace nauyin gawa,Haneef ya Masa tsawa yace fita ka bar nan,Iro ya fice a tamanin Yana cewa ni Kam naji dadi dama nauyi ne da ita. Haneef yace Me ya faru da ita Yana tattaba Jikin Khadija,Salamatu tace ranka ya dade yanzu kace ba kyau ka Kori Iro sabo da ya dauke ta Kai Kuma kana ta tattaba jikinta,Haneef yace ni na daban ne,ni da Iro daya ne? tace a'a yace to bana son sa Ido zan iya sallamar mutum daga aiki,Salamatu tayi shuru tace dama matarka ce ta turota daga bene,Haneef daukan Khadija yayi kamar tsinke ya fice da ita ya sata a mota,Iro hannu ya dora a ka yace Oga kamar dangin samudawa ji yanda ya dakko ta kamar buhun auduka ba wani wahala. Asibiti Haneef ya Kai Mero Allah ya kiyaye Bata karye ba amma wani wajen kasusuwanta sun tsage wani Kuma kashin ya goce da sauransu a ranar ya biya komai aka gyara Mero Inda za ayi dressing aka yi mata komai,ta Sha wahala wajen gyaran,Likita yace sai tayi kwana uku sannan a sallameta,Mero tana kwance a Saman bed Kafafunta da hannaye duk ya Sha gyara,Haneef ya kalleta ya furta sannu tace yawwa sai hawaye sharrr,yace to mene na kukan gani fa ni zanyi jinyar ki,Yanzu ma gida zanje tunda ga Salamatu in nayi wanka Sai na dawo kinji,Kai ta daga Masa,Salamatu tace Ina Nan zan kwana ma a wajenta yanlabai,Mero tace a'a ni ko babata ce tayi zamanta gaskiya ga abokina ya fiye min,Salamatu tace uhm ai shi yasa matarsa ta jefa ki a wannan halin. Washe gari Arham za a daurawa Aure kowa a dingi sai shiri ake yi duk da ba yanzu za ayi bikin ba,Ango kuwa Papa ne ya kira shi 'Yan uwansu na kauye Dattijai sunzo sun cika palon Papa, dukkan mazan gidan yaran Papa suna nan su Spark kaf an kira su a gaisa da Yan uwa na kauye,Arham ne kawai baya ciki sai yanzu ya shugo palon,Papa yace yawwa ga Angon ma shine Ango ai na gaji da halinsa, tashen balaga yake ji da ita Yana neman ya lalata yaran jama'a shi yasa nace a daura Masa auren kawai a huta,yaran jama'a yake bi kamar fan akuya gashi Nan kun ganshi na gaji da halinsa,Dattijan kauye suka saki salati da sallalami, Kai dai baka ji dadin halinka ba,wani tsohon yace da ganinsa anga tsagera wannan dama bazai kyale mata ba,Spark yayi dariya da su Rafeeq,Ai dama idan da hali in kaga yara na irin wannan sun taso da lalata haka kawai ayi musu aure shine maganinsu,na masara ma ya ishe su,da siyen Maggi aka barsu ma shike nan kawai anyi maganinsu,sannan abinda suke hange gashi Nan a basu macen,kayi daidai ka kyauta General. Wani tsohon Shima yace ai duk yaran General haka suke Yan banza gasu nan a zaune kamar na kirki ba abinda baza su fada ba a gaban mutum wannan dan iskan ana cewa Da na biyu Shima babba ne to wallahi babban banza ne Spark kake ko wa,Rafeeq Yana dariya yace ni yanzu Allah ya shiryeni da matata nake yi tunda na samu kawar yi,Misam Yana jinsu baiyi magana ba waya ya daga Yana tambayar Chika ya dana yau me yaci kuwa?suna jinsa tsofaffin suka ce kunji ko sai kace yaron yazo duniya Allah ya shirya. sai da ya gama wayar sannan Papa yace a shirya lokaci ya kusa,Arham yace to tsohon kaya zan saka? tunda yi min auren za ayi ai kayan da zan sa ma kamata yayi a bani a dinke,yanzu ni da tsohon kaya zanje,gaskiya Indai tsohon kaya zan saka bazan je ba wlh,Papa yace akwai kayanku Kai da su Shaheed an dinko muku ai nasan hali shi yasa an gama komai suna bedroom dina ku dauka kuje ku shirya. Ango farar shadda aka Dinka Masa harda babbar riga ta zamani tayi kyau,su Shaheed kuwa wata kala ce me kyau daban,tafiya suka yi kowa yana shiri a gidan har mata sunyi wanka sun saka sutura me kyau,Yan uwan Mima kaf sunzo suna gidan,Naila da su Chika duk sun zo yanzu,na nesa ne basu zo ba sabo da bikin ba yanzu bane,Amarya Basma tana kwance tana ta baccin rana abinta ta manta ma ance yau za a daura aurenta. Katafaren masallacin ya cika abokan Arham sunzo da yawa duk da ba shiri abin,suna ciki gaba bayan an idar da Sallar Juma'a aka fara yanke sadaki,dangin Amarya da suka zo wani Dattijo da kanin baban Basma suka yanke dubu dari biyu,Arham Wanda kamar a sace shi sabo da kyau,bai taba kyau irin na yau ba ya Kalli Papa yace yanzu wannan har kudinta ya Kai haka,me ta sani sai tona asirin tsiya ita za a biya kudi haka,ko girkin kirki ta iya ne? daga tuwo,danwake,Dambu,wake da shinkafa,dafaduka nasan karshen kwarewar girkinta kenan,Papa Yana jinsa kamar bai ji ba yace kawo kudi karka bata mana lokaci ai kana da su,Arham yace to wa zanwa transfer? dangin Basma kaf babu me accnt,a accnt din Liman aka tura, nan take Liman yasa yaronsa ya ciro kudi a POS an cire dubu daya charges,Arham ya zaro dubu a aljihu yace ku ungo kar a bini bashi ace saura dubu daya, gashi Allah ya hana babu,suka karba aka cika kudi dai dai chass sannan Liman ya fara Khuduba,Arham yace Innillahi wa innailayhirrajun za a zargeni yanzu,Papa Yana jinsa abinda yake fada sabo da suna kusa gaf ba me ji sai Papa,Arham yana ji aka tambayi Ango Yana da wakili ko shi zai karbi aurensa,yace Ango ni zan karbi Abina tunda ba taimaka min da sadaki ba kuwa babu me karbin min aure yana magana Yana hararar Spark wai nai ce ya bari ya biya Masa Sadakin ba,Spark yayi murmushi kawai Arham ya karbi aurensa da kansa aka daura aure ana ta dariya Wanda suke kusa sunji me yace shi zai karbi aurensa tunda ba a taimaka Masa ba,ana daurawa Arham yace shike nan har an gama? aka ce ae an gama Kuma,yace Ina Tausayin Amarya Kun daura mata alakakai,bacci ma wlh sai an kwantar dani,Papa yace ka gaji ma ka kwanta da kanka ku tashi mu tafi. Arham ya fito ana ta gaisawa da shi ana Masa fatan Alkhairi,ana cewa to Ango ayi ta hakuri,Arham yace ba nine da hakuri ba Amarya ce" ita hakuri ya kama,Papa ya chaka wa Basma dansa,ai mu indai ka auri Dan gidanmu to an Chaka maka,Spark yace wlh karya kake mu matanmu ba a Chaka musu ba ka tambaye su kaji basu da kamar mu. Naila ce tace wai ni Ina Amarya ne? Mima tace tana ta bacci an tashe ta taki tashi, ni wannan ango da Amarya na rasa irinsu wlh,Naila ta nufi dakin Basma ta sameta ta wargaje kafa daya can daya nan tana bacci,Naila tace ke Basma tashi tana girgizata taki tashi,ruwa ta dakko ta watsa mata a fuska da sauri ta tashi tana Murza idanuwa,Naila tace an daura aurenki kina wani bacci sabo da shirmenki,ki tashi kiyi wanka,an daura Allah?Basma ta tamanya, Ke baki ji a jikinki ba? Naila ta ce, Basma tace naji me? ba abinda naji tab,ke ki tsaya ki nutsu aure shi daban ne fa ba irin wannan rayuwar ake yi ba,ki koyi sirri ba a fadar sirrin miji,ko me ya taba miki ko yace miki ba a fada shuru ake yi,duk yanda kuke da mutum ba a fadar sirrin miji,yanzu ya zama mijinki ki girmama shi ki Masa biyayya,ki kula da abinki,kiyi tattalinsa,karki barshi shi kadai,Yar hira da kalamai masu dadi,iya magana,Kinga kwalliya tsafta,in ya dawo ki rungume abinki ki chafe dan mijinki,kissa da kisisina,iya shagwaba, Basma tana Jin Naila tace kema baki wuce a fada miki haka ba,baki wuce ayi miki irin wannan fadan ba kina yarinyarki da nawa kika fini,Dan kin rigani aure,wa yasan me kike shukawa Spark din naki,yanzu da zai warware mana abinda kike Masa kare bazai ci ba,amma dai gaskiya kika fada min Kuma zanyi abinda kika ce,Naila dariya tayi Basma akwai son girma ita bata yarda ba baza a fita shekaru ba. Wato baki yarda da abinda nake fada miki ba ko? Basma tace na yarda Allah Aunty zanyi Kuma duk abinda kika ce Kuma zaki gani,Naila tace yawwa ko kefa,tace Kuma ai nace koma ba a daura aure ba ko me yayi min bazan fada ba tunda naga babansu masifaffe ne,Kai muna da siriki a wajen Nan,shi kadai watarana muzurai yake yanzu Kuma Mima a haka suka soyayya ei Aunty? Naila tace Ina zan sani wlh ki rufa mana asiri sirikan mu ne,Basma tace bamu yi dace ba,ni da nake so na samu lusarin siriki Wanda ana min in na kawo Kara zaice Basma kece da gaskiya Allah ya miki Albarka,sai na hadu da Soja,Naila tace to nidai ba ruwana wlh,Basma tace ke wato baza ki gulmar su ba? Ai Spark ya mallake ki,Kai Naila zaki ci gado in Spark ya mutu Allah kawota da wuri mutuwa tono dadi kekam,ni kuwa nawa Allah sarki da zai mutu ko tumuni bazan samu ba haka zan koma gidan iyayena naci ga da agolanci na babu ko bukka. Naila tace wlh da Spark ya mutu gwara a kwace komai nawa na duniya,ke nifa Ina Jin akan ya mutu gwara mu mutu tare ko na riga shi,Basma tace tab wlh da cewa za ayi na zaba shi zan tura musamman idan na haihu in na mutu mantawa zaiyi ya auri wata ga yarana na barsu ai gwara ni na zauna na kula da abina,Naila tace wlh tunda kike fadar haka Baki fara son Arham ba amma duk sanda kika fara sonsa zaki bani labari da kanki,Basma tace Ina sonsa fa nifa tunda yazo zance naji kwakwalwata ta kwance a kansa sabo da sai naji kamar kar ya tafi,sanda Papa ya Kore shi daga gidan Nan akan nono na" ji nayi kamar nasa wuka na yanke su na watsar,Naila ta dinga dariya,tace nonon naki? Ei ai kuwa na musu addua mace Allah yasa su motse su tamushe,Kullum na dinga ciwon Kai sabo da bana ganinsa tana fada tana mulmulawa Naila cinya da hannu,Naila tace kyale min cinya dan Allah haka,Basma tace Spark Yana shanawa wlh Laushi,Naila tace naji tashi kiyi wanka sai Ango yazo ko so kike ya ganki haka ba gayu? tace a'a bari nayi,ta mike ta shiga toilet. Su Chika ne da Ikhram suka shugo suna surutunsu har Basma ta fito a wanka,tace sai kallo na akeyi yanzu na shiga uku da kallo wajen mutane,kowa Amarya ce itace Amaryar she. Ikhram ta mike tace Allah daga surukar General da Mima ta tashi na gaji,nifa idan ba a gidana nake ba takura nake yi,Chika tace yanzu Nan duk yaran Mima sun dirka mana ciki wannan yara Kwai Yan Duniya,yanzu Mima baza taji kunya ba ace 'ya'yanka duk sunyiwa matansu ciki,Naila tace Banda ni,Basma tace wlh harda ke Munji labari,Chika tace da gaske? Naila tace ke daga nayi zazzabi ake min wannan hasashen,idan akwai ai zaku sani ma,Basma tace Kun San girman Allah cike ne da ita. A gurguje suka zabarwa Amarya kayan sawa Leshi ne fari kwal me tsada yaji dinki hadadde ta shirya sabo ne dal,dama Mima ta Dinka mata bata saka ba,Ikhram ce ta yi mata dauri da Yar kwalliya sama sama ta zuba kyau sosai tana kamshi,Naila tace to muje Palo,Basma tace bazan iya fita ba ni kunya nake ji kawai kawai sai na fita mu hada Ido da Mima shike nan tasan na zama surukarta,Danta zai dinga tabani sai naje ta ganni,dariya su cika suka yi,ke a yaran ma sakarai ce Basma mene abin kunya duk dangi ne waye bai sanki ba. Da kyar suka yaki Basma ta tashi suka fito,sai buya take a bayan su tana ja da baya tana rufe fuska,abokan Ango da dangi kaf suka shugo lokaci guda da yawansu kuwa sun cika Palo,Basma bayan Ikhram ta tsaya tana buya,Ikhram ta matsa aka ganta kowa ta kiriri, ta rasa Inda zata saka kanta,ta rufe idanuwanta gam,Ango ya kalleta kawai,abokan Ango yara dasu matasa suka fara pics dinsu har family,Amarya sai kunya take je,bayan an gama akace za a yiwa Amarya da Ango su kadai,Basma tace nidai surukaina suna nan bazan tsaya ba,Arham ya harareta tayi shuru ta tsaya ana dauka ta ko Ina,ana gamawa Basma ta zauna tana ta tunanin abinda Naila tace ta yiwa mijinta ita tunaninta tun yanzu zata fara aikin. Dangin Mima duk da yamma suka tafi ya rage sai surukan Mima sai yaranta su Spark suna gidan suna ta hira,Arham Yana ta sallamar baki,Basma daga ji Mima tace yau Arham tun safe Bai ci komai ba ma,Basma ta tuna tace ance na dinga kula da shi Kuma,tashi tayi sum sum ta shige kitchen ta dinga bincike a kitchen tana zabo kwanika,wani sabon kwali da ba a bude ba ta farke flask ne sababbi masu masifar kyau da tsada,Basma tace irinsu ne na me gida ta zazzabo abinta tace sun da ce da shi. Sai na samu na gyara Masa gashinsa to ya zanyi ance na chafe shi dole na chafe shi nace cika masakinka Dan Arham,bari ya shugo. AsmaBaffa [2/24, 9:10 PM] AsmaBaffa: 🏫TANTIRIYA🏫 A GIDAN YARI BOOK 3 ~TAIMAKO~ 41-45 Official By AsmaBaffa Page naki ne Mrs Muhammad *ZINARIYAR MACE⚡* *Wai shin 'yar'uwa menene matsalarki? zubewar nono, ko kuma rashin kwankwason juyawa a falo maigida ya shiririce ya manta da tibi da matan tictok, menene matsalarki ne? rashin ni'ima ko kuma mugun sanyin da ya yi miki katutu, shin rashin taushin fata ne ko kuma kuraje da tabbani, ko bala'in ramar da ta addabeki kuma babu rashin ci ba rashin sha a gidan auranki, gwaigwayewar gashi ce matsalarki ko kuma kaushi da faso na tafin kafa da bushewar fata, kina bukatar fatarki ta yi glowing kalarki ta fita kuraje su mutu, ko kuma kina bukatar azababbun turaruka da humra tare da turarukan wuta. Na san dai kuna da yawa matan da tumbi ya yi musu karan tsaye ina nufin ya katse muku hanzarin yi wa maigida gwalli da muskuce-muskuce a falo😃 Nesa fa ta zo kusa AL-KUTUBIYYA ISLAMIC MEDICINE sun tanadar muku da nau'in magungunan da suke magance kowace irin matsala da izinin Allah. Babban burinmu shine sha'ani na aure ya inganta a samu daidaito. Muna da.* Na gyaran nono. Na sanyi. Dilka tare da hadin sabulu. Duk Wani nau'in maganin mata. Humra turarukan wuta perfumes, original miski tahra 3in1, ciccibi budurwar kaza. Had'addun supplement irin wad'anda ba su da matsala. Maganin Sliming wato narka tumbi. Abubuwan da muke sayarwa suna da yawa, kuma babu asarar dukiya. Muna garin kano kuma muna tura kayanmu kowane gari fad'in Najeria da Nijar har ma da kasashemn ketare. Kai tsaye a tuntu'bemu ta lambobin wayarmu domin karin bayani. *08089965176* *07084653262* Abincin ta zaba iri iri ta zuba Masa a flasks ta shirya komai abinta,Mima ce ta shugo ta Kalli abinda Basma tayi tace wa yace ki dakko wannan flask din? Wa ya aike ki? Kin San na mene ne? satin nan fa na siye shi zan kaiwa wata matar Senator gudun mowa zata aurar da yarta shine kika dakko kika wanke tare da zuba abinci,wa zaki bawa? Wanne baki kika yi?Basma tayi shuru,tambayarki nake yi nidai nasan a dangin ki ma ba wanda yazo,Basma tace dama Arham ne yace a bawa Yar aiki ta kaiwa wani abokinsa yazo daga nesa shine na zuba a nan sabo da ya fita kunya,naku ne flask din? Ki bari in aka kaiki gidanki sai kiyi Iko da kayanki,juye ki bani flask Dina,Basma kuka zata yi tace wlh idan aka kwace sai nayi zuciya a gidan nan,ko na fadawa Papa a bar min shi flask din,shi Papa sai ya biya kudinsa shike nan ya zama nawa,wlh da haka aka yi ma na huta ya biyani kudina cewar Mima,Basma tace to mun karbi bashi Mima zan karbi kudin sai na baki,Hakan yayi Ina jira Mima ta furta,tace to. Masu aiki ne suka shugo suka fara sabon girki,Basma ta juye waccen abincin tace wannan dama ya tsufa ayi sabo a zuba min a Nan,ta wanke flask dukkansu tace gashi wannan duk abinda ya dace a zuba min daban special,suka ce to Amarya. Tana fita taga yan mata sun cika Palo wai duk Yan secondary school da Yan University din su Arham ne suka zo Masa murna,sun ci wanka ga abokai Maza suma Yan makaranta,Basma ta zauna tana cewa nidai bani da kawaye a garin Nan,friends din mijinki ne suka zo muku murna,Basma ta tabe baki a ranta tace Allah yasa dai bai taba musu nono ba,gaisawa aka yi aka nuna musu Amarya,suka dinga yabawa suna Allah ya sanya Alkhairi,Basma tana amsawa tana murmushin yake. Arham ne ya fito" Basma tana ganinsa ta mike tsaye,Yan mata suna tsokanarsa Ango wlh munyi mamaki wai aure aka yi Maka,duk abokai har mata ba Wanda yayi aure cikinmu mu da muke mata ma sai muka ji Abu katsam,Basma kusa da Arham ta tsaya ana kallonta ko kunya,kishi take,kafin ya basu amsa tace farin jini ne da shi yayi kasuwa,baiyi kwantai ba shi yasa,Kuma shine baya ji shi yasa aka zarge mu da igiya sabo da na gyara shi ya zama mutum,dariya suka yi Dake Yan matan birni ne wayayyu ba mace ba namiji taba Jikin juna suke su tafa su rike hannu wai duk normal ne su ga yan Abuja,Basma tana kallo a garin abinda akeyi shi yasa baza a taba mata miji ba,wata a friends tace da Arham Dan duniya ta Miko hannu zata rike shi,Basma ta janye hannun Arham,tace wai ku bakwa tsoron zunubi ne,duk irin wannan Yan kana nan laifin da ake Gani a ba komai bane wlh sai su taru su yiwa mutum yawa,ana magana kuce Kun waye,duk wayewar da ba ta bin hanyar Allah bace aikin banza ce,nidai ku taba wani wannan an bada shi ato. Chika ce tace ki kyale bawan Allah da abokansa Basma,Arham kallon Basma yayi ta cukule ta turo baki,murmushi yayi yace gyara bakin to yanzu zasu tafi ma,Basma tace ni yanzu nayi course a wajen Siriki na muzurai zan dinga yi,Arham yace Papa? tace ae mana Ina da siriki Soja ace bana muzurai ai nayi asara,Mima ce ta fito da sauri Basma ta koma kujera ta zauna tare da fuskewa,Kawaye suka ce to taso ayi pics Amarya,tana shagwaba ta mike kamar sune Angon a haka aka yi pics,sun dan dade sannan suka tafi. Mima ce tace Kaci abinci kuwa? Arham yace kika ce baki damu dani ba,tambayarka nayi ni,Basma tace na zuba da zan Kai Masa sai naga suna yin sabon abinci shine na fasa bashi tsohon abinci, yanzu sabon nake jira,Mima tace yayi masu iyawa shike nan da abinci gasu Nan iri iri duk baza a bashi ba sai anyi sabo,haka zai ta zama da yunwa kenan? Basma tace sai da na tambaye shi ai idan Yana da ulcer yace kalau yake shi,shine yasa nace a bari ayi me zafi,dariya Rafeeq yayi yace wani ya shiga uku,Arham ya harare shi da wasa ya wuce ciki,Basma ta mike a ranta tace bari naje na chafe shi,Maman Rafeeq ce tace gidan uban wa zaki je Kuma? Wannan yarinyar idan ba a taka mata birki ba wlh kafin a kaita gidansa tayi ciki,Basma a hankali yanda ba me ji tace ke kin kashe aurenki kinki zama zaki kashe mana namu auren za ace baza muyi biyayya ba,Ikhram tace Kinga Basma jeki ki Kai Masa abincin naga kina mimimi da baki,Basma tace ko minti biyar bazan ba zan dawo,sabo da iyayensa kar su ga bana kula da dansu suce baiyi dace ba Nima ala dole zan Kai,Spark yace Dan Allah jeki kina ta surutu wa ya hanaki ne,ta tafi abinta ta shige kitchen tana zuwa an gama wani girkin ta zuzzuba sai ga Arham ya shugo kitchen din da kansa,tace kaga abincin fa yanzu zan kawo,Arham yace abinka da baka Saba ba ni a barni na eba da kaina,Basma tace wlh bazai yuwu ba kace wani baka Saba ba,yace duk wannan abubuwan wa zai cinye? Basma tace Kaine muje ta tura shi waje muje,Arham yace dole zaki min,ni karki shugo min rayuwa na tabaki kije ki fadawa mutane,Nayi Dan hankali zan iya kin fadawa Papa da Mima amma banyi alkawari ba zan iya canja ra'ayina kana bani haushi zan fada,Arham yace zan saita miki bakin ai wlh,ta dauki abincin suka tafi suna zuwa dakinsa taga Junior a ciki,tace Kai junior ka daina zuwa Nan yanzu kowa yayi zamansa a dakinsa yanzu ba sa'anka bane Arham Kai da Shaheed ku dinga taka tsantsan da shiga dakin nan,Junior yayi dariya yace dama yau dinma tsautsayi ne,to tashi ka tafi naka,yace to ba musu,tace ka samo taka a Mami market dinku ta sojoji tunda Kai dole sai ka zama Soja,Junior ya dauki laptop dinsa ya fice Yana dariya. Basma ta fara tunanin ta ya zata chafe shi tace gashi Kato ne ashe,tsaki ta ja a ranta,tace ita Naila ta ya take chafe Spark ne ita,Arham Yana kallonta Yana tsince tissue da aka watsar a dakinsa,Basma ta koma kusa da shi ya mike ya juyo zai tafi ta Masa kamar zata dauki yaro karami hannayenta a saitin hammatarsa tayi tayi ta iya ko motsa shi ta kasa,ta fara cika...ci ..cik...cikaaaaaa.....uhmmmm... ta durkusa a kasa zata daga shi wai ta kafafunsa,tayi nishi ta dage ta kasa,gumi ta hada nan take,Arham Yana kallon ikon Allah yace mene haka? dagowa tayi tace na kasa Cika masakinka zan Maka na dagaka na cafeka shine na kasa,Arham yayi dariya yace kin makara Mima ta Dade da yi min abina tun Ina jariri har aka yaye ni,kawai kace kana min bakin cikin shiga Aljanna baza ka nuna min yanda zanyi ba,Arham yace ai sai an kwanta akeyi,Baki ta tabe tace to yaushe za a kwanta? yace yanzu ma tace to ci abincin Dan wallahi yau sai na kaddamar zan tafi. Arham ya zauna a gefen bed harda zuba Masa abincin,yace yarinya ta fara cin Sadakin ta ashe dai da alama zaki ci kudinki 200k,wai haka aka biya dama? Arham yace ba a Baki ba? tace ae ni ba a bani ba ko sisi,yace tab tsaya naci abinci wlh baza ta sabu ba a baki abinki so ake auren ya dinga rawa ba a bawa Amarya sadaki ba Ina aure,Basma ta zauna a gefen bed tace lallai ma Kawu Dan Yana kanin ubana shi aka aura ko shi za a yiwa ciki,Arham ya sheke da dariya,yace kura da Shan bugu gardi da kwashe kudi,aje a bi min hakkina kar Kawu ya tafi kauye ba mutunci ne da shi ba,sanda Babana ya mutu ai kasa rike ni yayi,yace bazai iya ba sai yanzu anga na girma an bani sadaki na zai cinye min,sanda Ina yarinya ko fitsari nayi sai ya dinga dukana dole babata ta tafi dani agolanci shine yanzu yaji kudi yayi shuru Yana so ya samfe da su gida aje a siyi Masara a ci tuwo ni Ina nan an yi min ciki yau yawu gobe amai wlh bazan yarda ba. Arham Yana ta dariya yace wai ke shekarunki nawa ne? tace 17yrs da wuri na gama makarantar secondary sabo da karatun kauye sai a hankali,Arham yace a dawo maganar sadaki fa,tace ai dole na karbo abina Kuma a jikina zan cinye ba wata kadara da zan siya in samu in ta siyan kayan dadi,Arham yace wanne kayan dadi gashi kullum kina ci,tace ni dai a jikina zasu kare kudin,yace uhm uhm Basma dollar tayi tashin gwauron zabi,ba ruwana ni cewar Basma" ta sa hannu ta goge masa gefen bakinsa da dan abinci ya bata, suna zaune ya ci abincinsa ya shiga wanka,Dan kwanciya tayi a gadon tace bari ya fito sai naje na nemi Kawu ya bani sadaki na,kwanciya tayi daga rufe Ido sai bacci,baccin tsiya ne da Basma kamar me cutar bacci. Yana fitowa ya ga tana bacci ta Kalli sama,Maman Rafeeq kuwa zuwa tayi ta fadawa Mima tace tunda Basma ta tafi Kai abinci taki dawowa wlh tana can Kuma kin San yaran Nan musamman Arham din,Mima ta idar da Sallah tace jeki mana ki Koro ta ko gyaran Jikin ba a yi mata ba,Maman Rafeeq taje dakin Arham ta dinga knocking yaki magana Kuma yaki budewa kamar ba mutum,tace Arham Kai ...shuru yayi Yana Jikin mudubi Yana fesa turare tace baza ka bude kofar ba,magana yayi yace bacci nake na gaji da sallamar baki,Ina Basma ta fito,yace ai ta fita,karya kake ka bude tun kafin ranka ya baci na kira ubanka yazo da kansa,kofar ya bude ta hango Basma kalau tana bacci,tace tashe ta ta fito ke Basma ta shige ciki tare da jijjiga ta,Basma ta mike ta fito,Mama ta taso keyarta gaba. Ba ayi miki gyaran jiki ba kike wani Kai kanki wajen namiji daga aure,ai Kya bari shi ya nemeki,Basma tace to na bari Allah ya kawo shi tunda bakwa so nayi biyayya shike nan na fadawa Papa kawai,Mama tace sabo da shi ya kawo ki ana miki Abu sai kice zaki fada Masa to dukan mu zaiyi ko me, Basma tana jinsu ana mata surutu ta wuce dakinta. Tun daga ranar bata Kuma kula Arham ba,Mima tana kallonta ko ance Arham baici abinci ba bata magana,idan yace tazo baza ta je ba,har aka kwashe kwanaki hudu zuwa biyar,Mima da kanta taga zata raina Arham,ba abinda ake sa Basma tayi indai na Arham ne to kuwa baza tayi ba. Tana zaune a Palo yau duk su Mima suna nan Arham yace Mima ya naga ba a gyara min bedroom dina ba? na manta ma ban sa an gyara ba, ga Basma taje ta gyara,Basma tace to kawai taki tashi tayi zamanta,Mima tace ba Dake nake ba wai me kike yi haka mijinki ne fa amma ba a isa a saki aikinsa kiyi ba. Basma tace cewa fa kuka yi Ina Kai kaina wajen namiji na daina zuwa,in naje abinci zan Kai sai an biyo sawu na an Koro ni ana min fada Ina dalili ba sai na barshi ba tunda bakwa so,dama ni fada Aunty Naila ta min shi yasa nayi kokarin yin abinda tace Amma tunda kuka ce Ina zubar da ajina shi yasa na daina yi. Mima tace au Ashe zuciya kika yi kenan? Ae zuciya nayi,duk yanda na Kai ga sonsa bai kai ya ku ba kuka ce bakwa so a kula da shi a barshi yaci gaba da gwaurantakarsa shine nace to na huta,Arham yace banga laifinka ba kinyi dai dai Ina bayanki,Mima ta kalle su tace shike nan Basma yanzu ba ruwan mu ki kula da mijinki,komai kece zaki dinga yi Masa a gidan nan baza a sake bin sawunki ba,Basma tace a ranta sunji wuya sunga zan raina dan su,lallabata Mima tayi tace yanzu kije ki gyara dakin amma karki Dade bana so wani Abu ya faru tun yanzu,tace to ta mike ta tafi,Arham ya Kalli Mima yace na fuskanci a gidan nan da gaske ba a kaunata ni a bani gidana na tafi wlh,Ashe kune kuke hanata yarinya tana so ta bi mijinta sau da kafa,Mima tace je ka fadawa Ubanka ya baka gidan naka idan ka isa. Bedroom dinsa ya shiga Yana murna dan shi Kam hira da Basma ko da shiriritarta yana so,a Jikin Mirror ya gant ta tsaya tana shiryawa ya shugo" a bayanta ya tsaya ya dauketa chak yace Chika masakinka Yar Basma....dariya take yi hannayensa duka suna ta kirjinta a haka ya dagata Yana direta Yana dagata,Yana latse mata kirji an mata wayo,tace sai nayi Maka nima,ya daga hannaye ta kasa tace to ni yi min,ya jata Saman bed suka fada yace kyale gyaran nan muyi bacci,dama ke sarkin bacci ce,ya rufa musu bargo suka shige ciki,ya fara lallaba Basma yace dama mun cire kayan mu,tace kaiiiiiii ba ruwana,ba abinda zai faru fa,Kuma Lada zaki samu haba Yar Basmeme Yar kyakyawa,kace da bani da kyau,karya nake kina da shi sharrin shedan ne,Sai da ka cire min wlh dazu da zan saka kayan nan na sha wahala, Allah bazan yi wahalar cirewa ba sai dai ka cire min,ni bazai bani wahala ba zan cire cewar Arham,a hankali ya zuge zip din ya cire mata fitted gown din. Zai cire bra tace banda su,to shike nan ladan da zamu samu kadan ne, tace baza dai ka kula su ba ko? Yace mahaukacin inane ni zan kulasu,tace to cire ni ba ruwana,Arham yace ni da ruwana ya cire bra,pant ta hana taki yarda,idonta ta rufe ruf tace bazan sake kallonka ba kunya nake ji sai ka gama kallo zan bude idona,Arham yace kinfi yin kyau ma a haka,Arham duk ya rude yace wlh Papa idonsa na Gani tarrr sai kace an nuna masa,Ashe zabe ya zauna yi min,Basma tace a haka idon Papa mitsi mitsi Allah kamar na zabiya,Arham yayi dariya yace ko mun gado shi,tace Allah ya taimake ku baku gaji idonsa ba,ko kurar yaki ce ta Maida Masa idon haka oho. To wa ya sani ne shi yasa na gudu daga Soja cewar Arham,Yana Zalama ya Kai hannaye kirjin Basma,ta saki ajiyar zuciya tace kamar na yini Ina kuka ni dai,Arham ya maze Yar dariyarsa Yana so yayi mata wayo,sai kace an jona Masa wayar lantarki haka jikinsa ke rawa,Ya fara murje Boobs din Basma son ransa,bakinsa yasa ya fara tsotse daya,Basma tayi luf taji dadi,harda cewa ayiwa wannan Shima Allah sarki an ware shi ba a kaunarsa,Allah ayi Masa kar waccen a zuke shi ya gaji ya dangale ya bar wannan Kato,ai sai ya dawo kuturu,zai iya kuturcewa. Mima bata so Arham yayi komai gwara a gyara ta a kaita gidanta shine suka ga shuru taki dawowa,Maman Rafeeq tazo ta bubbuga kofa,Arham yace na shiga uku ni dai,Basma tace zanyi zuciya wlh,yace dan Allah karki yi,tace ni gaskiya zan fada a daina zuwa, Mama tace Arham ka bude kofar nan ko naci mutuncinka,Basma tace na fada? Yace fadi suji kunya su daina zuwa,Basma tace yar tabe muke yi,Maman Rafeeq taji kunya tana Jikin kofa,Arham ne yazo Jikin kofar yace Mama gaskiya ki koma gidan Rafeeq,gori zaka min Arham? Yana daga ciki yace to ki koma wajen mijinki Allah na gani,ka bude ka sallami yarinya bama son iskanci ko na turo Mima da kanta ai ita ka bude mata,Basma ce ta taso tana saka rigarta Bata zuge zip din ba ta bude kofa zip a bude tace gani Mama,fisgo ta Mama tayi tace muje,Baki ta bude ganin zip a bude tace zip din kika bari ya bude? tace ai yanzu na saka rigar zigidir nake dazu,Mama tace tab Allah ya shirye ku,Arham Yana ji yace baza mu shiryu ba tunda da aure wannan addua baza ta karbu ba,muje ta tasa keyar Basma zip a bude,tace baza ki gyara zip din naki ba? Basma ta gyara da kyar,Mima ta gansu tare da Mama,tace ke Basma baki san ya kamata ba? Idan ance kiyi Abu sai ki wuce gona da iri,idan ya miki ciki tun Baki tare ba fa? Ni anko nake so muyi da su Chika, sai ganina suke yi a yarinya Kuma ma ba abinda muka yi dama valentine da ya wuce shi muke yin namu yanzu,lokacin Ina kauye ma Valentine yazo,rufe min baki ki bani waje,Basma ta haura sama,Mama tace ke nifa yaran nan na gaji wlh a gabana tace Yar tabe suke yi zip a bude ta fito,Mima tace ai wlh nasan za a rina General ne baya Jin shawara,ai watarana a palon nan zasu yi na fada miki,Kinga Arham hmm ni naga me na gani. Zuwa dare Arham yaga kowa ya kwanta ya wuce ya tafi dakin Basma,dakin ya shiga yaga Haly a ciki suna kwance tare,Haly ya tasa yace San Inda dare ya miki,Haly tace ban gane ba wlh zan fadawa Mima ai ance ka bari ayi biki a kaita shine kazo,Basma ce ta bude Ido tace wannan fa ubane a wajenki idan ba ran Papa sune Iyayenku,kibi umarninsa kawai,Arham yace Haly Baby ya mata signa,tashi tayi yace ki dinke bakinki,Haly tayi murmushi ta fita. Basma tace ka sa key kar su fado ciki,ya mike ya sa key ya dawo tare da haurawa Saman bed din,tana kwance ya Maida kansa Saman kirjinta. Khadija tana asibiti zuwa dare Haneef ya dawo asibitin da tarkacen jinya komai na bukata sai da ya kawo Yana zuwa ya sallami Salamatu yace jeki gidan ni Sam ban yarda da Ihsan ba kije ki sa min Ido,tace to,Ihsan kuwa ganin ya kwashi tarkacen zaman jinya tace bari na kira Sadeeq yazo ya tayani hira,tunda wata kake kulawa Dan me ni zan zauna Ina jiranka Nima bazan nemi me faranta min rai ba,wayar Sadeeq ta kira bugu daya ya daga,yace Hajjaju ya gida ya aiki? tace Alhmdllh,na gode da da karamcin da kika min yau,tace ba damuwa da Allah naga dare baiyi ba ko zaka iya siyo min wani nama ka kawo min gida yanzu zan tura ma kudin,yace ba damuwa ba matsala Hajiya,tura min accnt dinka,Nan take ya tura mata tayi Masa transfer na 10k tace na 2k zaka siyo min sauran ka rike,ya dinga zuba godiya yaje ya siyo mata, address ta tura Masa ya kawo mata Naman har gida,yayi mamakin girman gidan da irin haduwar gidan,sai kallon gidan yake,a Palo ya sameta sanye cikin kana Nan kaya riga da wando,kallonta ya sata kawai ta birge shi,tace ka zauna mana,zama yayi yace gidanki yayi kyau,yanzu duk gidan Nan ke kadai ce kike zama? tace daga ni sai Yar aiki na,gida nane yayi kyau ko? yace sosai ma kuwa kin more sai dai a Yar bahaushe Musulmi bai dace ace kina zama ke kadai ba sai Yar aiki,Ihsan tace aiki ya kawo ni,mikewa yayi yace zan tafi,tace nooo...zauna please Kaci wani Abu Kuma ma ka zauna ka Dan debe min kewa,Baki ya bude yace what? ta furta ba kyauta zaka min ba biyanka zanyi,zan baka 50k ka zauna muyi hira kawai,yace kawai hira 50k? tace ae mana,sai nayi kwana nawa a duniya ban samu 50k ba gaskiya na gode,kitchen ta shiga ta kawo Masa abinci ga Naman da ya kawo tace muci tare,Yana dan tsoro haka suka dinga cin abincin tare suna hira suna sheka dariya. Tace to fada min me kake yi na sana'a,sannan mene tarihinka da asalinka? yayi murmushi yace iyayena sun rasu tun Ina karami,daga kauyenmu Kebbi na dawo birni neman aiki,Ina Fadi tashi Allah ya taimake ni wani me kudi ya bani kurkura Ina ja,da dakina da na kama haya a wata quarters Ina manage sannan Ina tare da kakata Ina kula da ita. Tace mashaallah wannan aikin naka ai bazai isheka komai ba,bubu kudi da yawa me zai Maka wannan Dan kudin, ka bari inshaallah za a San yanda za ayi,Yana ta godiya Salamatu ta dawo,tsaki Ihsan tayi ta share Salamatu suka ci gaba da hira da Sadeeq din suna hirar su suna dariya cike da nishadi,yana kare mata kallo ta Masa kyau matuka,sai yaji ta birge shi sosai ta tafi da Imaninsa,Salamatu tana kallo tace cab wannan ai dai baza ace dan Uwan Aunty bane. Haneef kuwa Salamatu tana tafiya ya zauna a kujera a gaban Khadija Yana kallonta yanda ta tararrabe tana shagwaba,Khadija tace ni dai gidanmu zan koma gwara na koma naci gaba da cin awara ta da Koko na akan matarka ta nakasa ni,duk ta rugugguje min kasusuwa na,kiyi hakuri ke ya aka yi kin San halinta kika biyo hanya tare da ita? ai ban San bata da Imani ba haka,wlh duk tsanar da nayiwa mutum bazan iya yi Masa haka ba yanzu da na fado a ba daidai ba gida gida fa zan karye ko Kuma hakora na duk na rasa su ko na mutu ma ko wuyana ya karye,to Allah ya kiyaye hakan bata faru ba ma,kiyi hakuri kinji ya furta Yana taba wuyanta,Mero tace bazan Kuma kulaka a gabanta ba bata da hankali wlh mahaukaciya ka aura. Haneef ya boye dariyarsa Jin Khadija tace baza ta sake kula shi a gaban Ihsan ba,yace yanzu kin yarda ta raba mu kenan? Shike nan Yar hirar da muke da abincin da muke ci tare shike nan? Mero tace ai lafiya tafi komai,sai ta halaka ni sai dai na kula ka a boye a munafunce,dariyar Haneef sai da ta fito fili yace I'm sorry kinji tashi ki dan Sha fruits,Khadija tace a dagani bazan iya ba Naman cinyata ya tsage,Mikewa yayi ya dagota ta saki Kara ta rungumo shi gaba daya ,Haneef jikinsa yaji wani yarrr....ko Ina ya amsa kamar kar Khadija ta sake shi,ya sake kankame ta ya bige da lallashi,kirjinta gaba daya a jikinsa gashi ba bra,tace to bari na gyara,yace tsaya a haka ki huta...huta...huta....ai irin wannan sai ki karasa aikin da aka yi,Khadija ciwon nata bai kai haka ba amma ta sake narkewa tana shakar kamshinsa harda cewa ba muharramina bane amma ai lalura ce,yace Lalura ce ko Likita ta kama haka zai miki Kuma duk Yana cikin lalura bare ni dan zaman jinya,Khadija tace na huta haka ai zan iya zama,ki Kara hutawa dai sosai,suka yi luf a haka har sai da nurse ta shugo ya saketa,tace kana ji da matar nan taka. Zama Khadija ya bude take away din da ya kawo mata da fruits ya sa spoon Yana zaune a gabanta kamar zai shige jikinta ya shiga bata a baki tana ci,Khadija a ranta tace Ihsan ta jawowa kanta mijin ya dawo wajena jinya,Haneef kuwa Yana Bata abincin Yana kare mata kallo,Khadija tace mene ne kake kallo na? sharewa yayi yace ba komai kina da kirki ne na Mori Kawa,tace hmm tana murmushi. Ihsan kuwa Sadeeq Yana tafiya ta wuce bedroom ta kwanta tana furta what man can do woman can do better wlh,ka kula wata ba kula wani Nima. Abba ne ya shugo gidan ana gobe sunan Beauty,Naila tazo,Chika,Ikhram,Hidaya,Iman duk suna nan sune a gidan suna zaune a dakin me jego sun cika gidan da hayaniya har tsila Hidaya anyi aure an shige cikin matan aure,Abba tun safe baya nan sai yanzu ya dawo yaji duk sun zo,ya leka dakin,Naila tace Oyoyo Abba,Abba yace sannunku duk kune haka sai kace mutane dubu ne a gidan,dariya suka yi suka gaisa Abba sosai yace to Kuma Allah ya baku naku masu albarka gaba dayan ku,suka ji kunya ya juya ko a jikinsa yayi gaba,Naila ta taso ta biyo shi,suka jero tace Abba tun safe nazo baka Nan,yace Yan barka ne suka takura min,baki ga na rame ba?ai sune suke takura min,abinci bana ci ya tsirga min,Naila tace ai an kusa ana yin suna shike nan,yace ya mijin naki? Naila tace Yana Nan lafiya yace a gaishe ku,ba wata matsala? tace ae,ba zagi,ba duka,ba cin mutunci? ya uwar mijin? Naila tace komai dai dai Abba Abu ya gyaru ba matsala,shike nan haka ake so ai Allah ya Kara zaman lafiya,Abba kaje Umma zata fada Maka wata magana kaje kaji,yace to,ya tafi kuwa Yana zuwa da Yan uwa su Goggo duk sun zo,ya zauna suka gaisa ya wuce dakinsa,Yar Inna ta shiga yace yau na yini ban ganki ba tun da rana nake Jin ciwon Kai amma yanzu har naji kamar na Sha Panadol,kece Panadol din zuciyata Yar Inna shugabar kyakyawan Dattijai,Yar Inna tayi dariya tace au bama shugabar mata kyawawan mata ba ta iya Dattijai ce? Su Naila sun tare wajen,in su Naila suna nan ai baza kizo wajen ba,kin haifi irin Naila Ina ke Ina zuwa wajen,Yaran nan zamani akwai iya zaben mata gasu Nan cikin daki duk babu banza a ciki,wannan tana wane wannan a kyau,Yar Hidayan ma da nake cewa ta gado ni tunda tayi aure ta canja gaba daya ta zabura tayi kyau,gashi nan har yanga take min,Naila ce take haba haba dani,amma ita waya take ma Kuma wlh nasan bazai wuce mijinta ba,shike nan na rasa 'yata"Nabeel ya rabani da ita. Hidaya ce tayi sallama ta shugo ta durkusa a gaban Abba,yace yanzu na gama gulmar ki kin daina son babanki sai miji,dariya Hidaya tayi tace ni na Isa Abba wlh Ina sonka,yace dadin baki ba,Yar Inna tace tana sonka mana, Hidaya jeki abinki,tana mikewa ta fita, Abba yaje yayi wanka yaci abinci,a daren Annoor yazo ya dauki matarsa,tayi tayi ya barta ta kwana yace wlh bazan iya ba muje gida ko gobe na hanaki zuwa suna" haka ta shiga mota ta bishi ,Hidaya kuwa cewa tayi zata kwana Abba yace wa nake ji tace zata kwana? Naila tace Hidaya ce,yace daga nesa kika zo ga baki ga hanci wlh sai kin tafi,tashi ki koma dakin mijinki da safe Kya dawo,Hidaya tace Abba ya barni fa,sai kin koma Hidaya bari yazo ya dauke ki,Nabeel dama duk gidan ya Masa wani iri bai so ya barta kwana ba amma ta tashi gaba da kuka sai da ya barta. Abba ne ya kira shi yace kazo ka dauki Hidaya mana Ina nan Ina gidanka da zaka barta ta kwana,Nabeel yaji wani dadi ya dinga godiya,yace Abba Allah ya Kara daukaka,Dan film ne ni ko kuwa wani Cele ne da zaka ce na daukaka,iya Yan unguwa da suka sanni shike nan,haka ma na godewa Allah,Nabeel yayi dariya yace to Alhmdllh Abba. Hidaya kamar tayi kuka,Naila tana ta mata dariya tace Ina murna zan sarara Abba ya bata komai,Naila tace uhmm su Hidaya yanzu ya wajen yake ne? Hidaya dariya tayi tace ni dai kin San ba Yar iska bace bana irin zancen ku tunda kuka zauna anan banjin kunyi hirar arziki ba. Haka Nabeel yazo ya dauki Hidaya Yana mata dariya Shima suka tafi gida. Abba ne ya tambayi Yar Inna me Naila tace ki fada min? Kubra tace wai fa ciki ne da ita wata uku,iya shegen Naila ne ai ba kunya take ji ba in Taga dama Kai zata fara fadawa ma,Abba yace Allah ya raba lafiya,ko wani Hashimu Dolon za a samu,Wlh ko namiji ta Haifa baza a saka sunanka ba shike nan kowa aka Haifa sai kace sunanka,yace na gaji ni kwanciya zanyi,ya kwanta tare da cewa da ke matar kirki ce ai da kin matsa min kasusuwana kin min tausa,tace to Yar Inna ta shiga yiwa Abba tausa,yace kin tuna min babata na taba kurenta Sanda Ina yaro tana yiwa Baffana tausa,Ina zuwa ta Kore ni tafi fura zan dama Masa,Yar Inna tana ta dariya. yace zan fada miki abin kunyar Baban Jauro kiji AsmaBaffa [2/26, 6:14 PM] AsmaBaffa: 🏫TANTIRIYA🏫 A GIDAN YARI BOOK 3 ~TAIMAKO~ 46-50 Official By AsmaBaffa SADAUKARWA NE GA AIDA MAMAN TASNIM PAGE NAKI NE Amatullah Kamshi *ZINARIYAR MACE⚡* *Wai shin 'yar'uwa menene matsalarki? zubewar nono, ko kuma rashin kwankwason juyawa a falo maigida ya shiririce ya manta da tibi da matan tictok, menene matsalarki ne? rashin ni'ima ko kuma mugun sanyin da ya yi miki katutu, shin rashin taushin fata ne ko kuma kuraje da tabbani, ko bala'in ramar da ta addabeki kuma babu rashin ci ba rashin sha a gidan auranki, gwaigwayewar gashi ce matsalarki ko kuma kaushi da faso na tafin kafa da bushewar fata, kina bukatar fatarki ta yi glowing kalarki ta fita kuraje su mutu, ko kuma kina bukatar azababbun turaruka da humra tare da turarukan wuta. Na san dai kuna da yawa matan da tumbi ya yi musu karan tsaye ina nufin ya katse muku hanzarin yi wa maigida gwalli da muskuce-muskuce a falo😃 Nesa fa ta zo kusa AL-KUTUBIYYA ISLAMIC MEDICINE sun tanadar muku da nau'in magungunan da suke magance kowace irin matsala da izinin Allah. Babban burinmu shine sha'ani na aure ya inganta a samu daidaito. Muna da.* Na gyaran nono. Na sanyi. Dilka tare da hadin sabulu. Duk Wani nau'in maganin mata. Humra turarukan wuta perfumes, original miski tahra 3in1, ciccibi budurwar kaza. Had'addun supplement irin wad'anda ba su da matsala. Maganin Sliming wato narka tumbi. Abubuwan da muke sayarwa suna da yawa, kuma babu asarar dukiya. Muna garin kano kuma muna tura kayanmu kowane gari fad'in Najeria da Nijar har ma da kasashemn ketare. Kai tsaye a tuntu'bemu ta lambobin wayarmu domin karin bayani. *08089965176* *07084653262* Yar Inna tace karka fada Dan Allah bawan Allah ya mutu da dadewa,Wa yace yayi sai na fada....Umma ce ta rufewa Abba baki da tafin hannu,yace ko ba yau ba sai watarana na fada,tana sakar Masa Baki yace Jauro da babansa suka nemi budurwa daya suka dinga fada a junansu,Jauro yace da Habiba idan babansa yazo ta fasa Masa Kai da dutse,shi Kuma Baban Jauro ya sa yaran unguwa suka dinga fesawa Jauro Mari.... Shewar su Naila yaji suna hira tayi dadi,Abba yace bazai wuce hirar mazajen su suke yi ba. Naila ce Spark ya kira ta yace yau ba Kwalbewa,Naila tace Kuma sai Nan da 3days zan dawo,yace ban yafe ba kwana daya na bayar gobe da wuri zanzo na dauke ki da kaina,Naila tace in kayi hakuri da kaina zan dawo,ban yarda ba Baby,kin San Allah ba wai maganar Kwalbewa ba kawai gidan babu dadi ba kowa da ma kin haihu ne sai ki bar min dana ko 'yata muna tare amma ba kowa ni kadai,Naila tana kashe Murya tace Baby,Spark yace Kai Ina Shan Baby Ina morewa wallahi,ga Baby Dan jakar uba Kato,dariya suka dinga yi su Chika sabo da suna Jin wayar me ake yi,tace dama dai kaga ka dade baka siya min komai ba,yace takalmi sabo ya fito kenan,Naila tace ba shi bane fa kamar zata yi kuka,Pleaseeeee....yace uhm Ina jinki,wani turare ne Babynka Kuma yaji kamshin yace Yana so,Spark yace a Ina yaji? Yana ciki ace yaji kamshi Yana so,komai aka tashi ace Baby ne,rannan kika ce yace a baki kudi,ni Gani ubansa idan so yake ya min magana da kansa,ki fada Masa ya sameni ni ubansa muyi magana,Ikhram suna ta dariya a boye an kure Naila,tace ai baza kaji muryarsa ba akwai wani Abu daga uwa sai da suke magana tun Yana ciki babu me Jin maganar sai uwarsa,Spark yace naji wannan karo wata,turare ne na daki Dana jiki,Dana ajiyar kaya,da na toilet etc,duk idan zan siya da dan yawa za a kashe 70k,baya fita kamshin,Spark Yana ji yace shi Dan ya bari a siya Masa ragon suna tukun,yace a yanka Masa ko bashi ne wannan yafi muhimmanci,Ina ATM din Dana baki? Naila tace na siyawa Baby kadara fili na siya Masa,Spark yace Dan Allah da gaske kike ko karya kike? Naila tace da gaske na cinye kudin Nan Amma ba kadara na siya ba,wai nawa ne kwata kwata a ciki,ni bana shanawa a gidan mijina,mene amfanin me kudin,Allah ya hore Maka dole naji dadi wannan kudi baza su dawo ba sisi bazan bayar ba na cinye,murmushi Spark yayi yace idan kin cinye ma ai kanki kika yiwa one Kobo bazan baki ba wlh,gwara na taimaki marasa karfi ke kina ci kina koshi,turare shine matsalarki,kin San ana ta kwana da yunwa wasu yanzu suna Nan suna cewa gari zai waye Ina ma a wuce gobe a tsallake ta a fada jibi sabo da wahala. Fushi Naila tayi tace kudin ba yawa fa kasan bazan kashe su a banza ba wlh,kaima kasan da dalili,to me kika yi da su fada min,Yan uwana na kauye na taimakawa aka siya musu kayan abinci na raba musu,yace wai kuwa Ina Malam Ya'u Dan caca Wanda ya cinye ki a caca? Naila tace so nake in muka je tare ya ganka,okay idan nazo daukanki gobe sai muje can mu kwana Daya,Naila tace ai su Goggo suna Nan mu bari sai sun koma,yace to ba damuwa,yanzu dai kudin turare zan bayar? Tace ae akwai wani takalmi Shima...bazan siya ba Shima turaren Dan Yana da muhimmanci ne,Naila tace dan Allah in na dawo zan baka bado sau ba adadi,Spark yace ko Baki bani ba ai zan kwata ta karfi, kawai bana so turaren ya wuce ni ban siya ba,Beauty ce ta samo mana me siyarwa,Yace to an gode mata za a siya,Beauty ta siya ma bare ni ko million ne sai na siya miki,Naila taji dadi tana murna tace ai na sani,nifa nayi dacen miji. Sun dade kafin su gama waya . Washe gari da safe a masallaci kafin ma Mohsin yazo Abba yasa an radawa yaro suna Hasheem,Naila tace ai dai baza a Fadi ubanmu ba sai a samo suna a Dan makala Masa na saka Masa Ashraf ai akwai ma'ana me kyau,Chika tace ba gwara Misam ba,Beauty tace duk kunci ubanku sunansa Annoor shi nake so,ba Annoor mijin Iman ba kawai sunan ne ya min tun da dadewa Ina son Sunan shi yasa,Iman tana zuwa taji ana cewa jariri Annoor tace Annoor Dina? Beauty tace ba shi ba a wanne dalili so kawai nake na saka Masa abina,Allah ya Masa Albarka,Iman tace a kasar Nan naga alama kowa a cikin fushi yake amma sai a dinga nuna a farin ciki ake kowa pretending yake Yana yake,Ina shugowa wata mata ta dinga masifa zan take ta wai,Naila tace Goggo ce fa suna dariya,Mohsin ko zuwa gidan baiyi ba ya barwa Abba komai a hannunsa an radawa yaro suna an yanka raguna uku manya. Sai da Beauty ta tsala wanka yazo gidan Abba yace sai yanzu kaga damar zuwa wai Kai me gida ka haihu ko,sai an jira ka nufinka?Mohsin yace to Abba gani nayi ka Isa komai a wajen shi yasa ban zo ba sai yanzu,Allah ya shiryeka Mohsin ga raguna Nan an yanka anyi komai,Kai Mohsin yanzu duk wannan ragunan na Beauty ne? Ina na sirikin Beauty? Zan fara hassada gaskiya,Mohsin dariya ya shiga yi yace ta Sanwa Siriki ko a plate ne,Allah ya kiyaye ai wlh da bazan karba ba,Allah sarki Yar Inna da kyar ta samu aka yi yanka a haihuwar Hidaya data Naila,lokacin muna tsananin babu sai babanta ne ya bamu rago,a haihuwar Hidaya,Naila kuwa Tinkiya aka yanka,Kai lokacin kana da gata an bar min gado rago biyu na yanka Maka,Mohsin yace shi yasa nake da Albarka,Abba yace ba wani nan,wlh idan Jauro Bai zo min Suna ba babu ni ba shi ko gidansa bazan sake zuwa ba naga har yanzu bai zo ba, Annoor kuwa da shi aka rada suna a masallacin mutumin da ban sa rai ba yafi surukin nawa ma Nabeel,sai na ganshi yazo shi da Haidar,sun kyauta ai cewar Mohsin,ciki ya shiga ya gaida Umma,Naila tana zaune tana kwalliya a tsakar gida da mudubi a hannu,gaisawa suka yi ya shiga dakin me jego kasancewar Safiya ce babu mutane sai yamma. Jauro da wuri yazo ya dauki Abba suka bar gidan suka tafi gidan Amaryar Jauro,Abba Yana zuwa yace shi yasa nake son Habiba wlh tana can ta tafi gidan Sunan jikanta amma ke kina nan gida, Jauro yace ban gane kana son Habiba ba wlh ko na rigaka mutuwa ka auri matata ban yafe Maka ba,Abba Dolo yayi dariya yace Allah sarki Habiba ba ajina bace duk matanka ba ajina a ciki,haba Jauro ai sai dai in na mutu kazo neman auren 'yar Inna Kuma wlh fatalwa zan Maka baza ka taba Jin dadi ba sai na dinga fito Maka a horror,duk Wanda na mutu ya auri Yar Inna ya gama Jin dadin duniya,bazan taba mutuwa gaba daya ba sai na dinga yin fatalwa,Jauro yace ka gaji ma ka mutu gaba daya din,yace in banda ma abinka Habiba ai Bata waye ba ko ka mutu ba abinda zanyi da Habiba sai dai na dinga kawo mata tallafin kayan abinci. Maman Annoor abinci ta kawo musu Jauro yace munci a gidan suna Yar Inna ta zubo mana girki,ga waina ga sinasir,ga tuwo ga shinkafa dafaduka ga Soyayyar shinkafa ta Sha koron wake da yelluwar Masara,girkin da su Habiba da Maman Annoor har a koma ga rabbana baza a iya ba cewar Abba,Maman Annoor Jauro Yana Jin Abba yace hmm wlh da zan iya daina Aboki da Kai da tafiya ta zanyi na daina kulaka kaddararren Aboki ka dame ni ka dami iyalina,Abba Yana Jin Jauro Yana surutu yace Jauro ka tuna Baffanka lokacin yana jinsa da jini a jika yace Habiba yake so,Jauro yayi dariya yace muka dinga takara muna fafatawa da Baffa akan Habiba,Abba yace an Dade ana abin kunya a duniya,Jauro yace na dinga gaba da shi nace da Habiba idan yazo zance kawai kar tayi tunanin Uba nane ta fasa Masa Kai,Ashe ya fini target ni Ina zuwa zancen yasa yaran unguwar suka Kwada min Mari yafi biyar,ranar da za'a daura aure naje na sace Habiba muka gudu,sai gashi ana rokona na dawo a daura Dani,lokacin ana tsoro kar na lalata ta,Habiba Kuma ita ga virgin me tsoron Allah,Komai aka yi Jauro ba kyau Allah ya hana,Miko min takalmi Allah ya Hana Jauro ni ba matarka bace babu kyau ka sa wata mata tayi Maka hidima,Maman Annoor tana dariya tana saurarensu. Sai yamma likis Annoor ya biyo daga wajen aiki ya kira Iman ta fito su tafi gida,sallama ta musu,Beauty ta bata kayan suna wani cake da tarkace a cikin wata jaka me kyau,ta shiga kwalawa Naila kira..Nailan Spark.....Nailan Spark nake nema ta leka wani daki...dai dai lokacin Spark ya shugo gidan tare da Mohsin,yaji ana kwalawa Naila kira Nailan Spark,yace ko wace wannan ta iya kiran Sunan, ya furta da kansa Nailan Spark sweet name,Iman ta sake kiran sunan Nailan Spark zan tafi,Spark yace ga dai Spark din Naila,murmushi tayi suka gaisa,yace kin iya saka suna,Naila ce ta fito tace Iman wai har tafiya? Yazo fa yana waje,Naila tace to ki gaida gida muna godiya In na dawo zanzo,Allah ya kawoki Beautyn Mohsin ta shiga wanka kice na ware na gode ta juya ta fita,tana zuwa Annoor yace Ina Hidaya? tace yau ana suna gidansu ai baza mu tafi tare ba,ban gane ba Dan Allah je kice ta fito mu tafi sauke ta zanyi a gida. Iman ta koma ta kira Hidaya tace ki taso mu tafi inji Sweet,Hidaya zata yi musu Naila tace in kin zauna uban me zaki wa wani ke ba aiki kike ba sai kwanciya, tashi ki tafi,Hidaya zata yi magana Naila ita a dole babba tace ki tashi ki tafi wlh wai wanne irin Abu ne wannan,tashi tayi kawai ta gaida Spark tace Umma na tafi,tun yanzu? to ya turo a daukeni ya zanyi Abba ya riga da ya bada ni,to ki gaida gida, ta fita suka tafi Iman tana gaban mota Hidaya tana baya suna ta hirarsu har Annoor. Amare kuwa Nabeela da Rahma shirye shiye suke yi Abu Yana ta tahowa kusa. Naila Shirin tafiya ta wuce tana yi,su Chika ma haka,Beauty tace Ina ma Nima a can nake tare da ku,Spark Yana wajen Umma bayan sun gaisa ya fita Yana jiran su,sallama suka yi suka tafi Zarah da ta rako Naila tace Aunty ki tafi dani,ki bari ayi hutu da kaina zanzo na dauke ki cewar Spark,Chika,Ikhram,Naila da Spark airport suka wuce,Spark ya gansu a hanya zasu jera da shi yace bazai yuwu ba kuyi gaba ku biyu ko baya ni da Baby muna tare,sai kace me mata uku sai kallona ake yi,Ikhram da Chika suka yi gaba Naila da Spark suna baya a haka suka shiga jirgi zuwa Abuja. Mummy ce zaune tare da Yar uwarta a gidan yari tace har yanzu Spark bai zo ya duba uwarsa ba tun Ina Jin wahalar rayuwa a gidan Nan har na fara Sabawa ma,Maman Wahida tace wannan yaro baida hali,Ina gidan nan yake zuwa wajen wata banza bazai neme ni ba,danki ba Dan mutunci bane,Mummy tayi murmushi ta furta haba Yaya duk yaran Mima akwai kamar Dana?gaskiya nasan da dalili amma zaizo ne,tunda Yana min aike ai da sauki,tabe baki Maman Wahida tayi,su biyu a gidan yari basa safgar kowa sun hade kansu suyi fada su shirya ba sa kula kowa su masu kudi ne,Mummy ma tafi saukin Kai sabo da ta canja hali sosai kafin a kawo ta gidan yari,Maman Wahida kuwa har yanzu da akidarta ta kudi ita me kudi ce. Naila suna komawa gida tace ya kamata Muje wajen Mummy har yanzu baka je ba fa,Spark Yana kwance yace Ina sane da ita bana so naje na ganta cikin damuwa ko naje na ganta a wani hali zan iya kuka,dariya Naila tayi tace Kai kuka baya Maka wahala a yanda Maza suke da karfin zuciya,kin taba ganin kuka na in banda akan Mummy? to yanzu a kaina baza kayi kuka ba kenan sai iya Mummy? Kishi kike da uwata dama ko,a'a ni na isa na hada kaina da ita ni a wa dorin dofino kunu bayan ludayi,rufa min asiri na mutu dakin uwata, akan me zan hada kaina da Iyayenka ai ko da Yan uwanka bazan hada kaina ba,ni da nake macen aure ko yaushe za a iya sakina,su kuwa fa Yan uwanka ne har abada Kuna tare,ni kuwa a gobe kace na tafi gidan ubana ya zama dole na tafi, ni dama bance na kaita ba,mu da aka auro mu a sama,ana ganin kamar taimaka mana aka yi mu gamu talakawa kullum kallon mu akeyi a taimaka mana aka yi ai,iyayen mu basu da shi,Spark tsayawa yayi Yana kallon Naila da mamaki,dakatarta yayi yace wait wait...yanzu Nan har kinyi fushi wai? daga Yar magana shike nan kin Fadi tafi Hamsim,komawa tayi jikin mudubi ta haye kan Inda ake jera kayan kwalliya tasan ba a zama a kan irinsa ba Dan kamar glass yake ai kuwa nan take ya fashe rukukus,ta tashi hankalinta sai neman masifa take, kayan ne babu Quality,ance za a min kayan daki akace ai an zuba komai gashi yanzu ko Shekara banyi ba sun fara fashewa,Spark ya kalleta kawai yace Allah ya shiryeki,tana jin haushi kamar an mata wani Abu,ficewa tayi taje kitchen ta dauki tire ta shirya abubuwan ci ta zauna a Palo tana ci,Spark ne ya ya fito ya Kalli tire din duk tarkace ne a ciki rakwacam,Bread take ci da kifi,ga Kuma Ayaba guda uku,lemon bawo Daya,ga ruwa ga lemo Mineral roba har biyu,ga Madara peak ta ruwa. Dariya ta bashi ya Kalli tire din yace wannan duk ke kadai zaki cinye? ya dauki kifin yana cewa duk yaushe kike soya kifin Nan ne baya karewa,Dan Allah ki rage ai sai cikinki ya lalace ya dauke madarar da lemo Mineral,kuka Naila ta fara,Dana Yana so yaci Kuma baza a bashi ba,Spark yayi dariya Don Naila yanzu ta haukace sai anyi hakuri da ita,yace cikin nan fa ciwon hauka ya sa miki Naila,Ina zaki Kai wannan tarkacen kin kula shi tayi tace Ina zaka je? fita zanyi yanzu zan dawo,ba Inda zaka je ka zauna tausa zaka min waye yace kayi min cikin wato Kai kullum sai dai kayi wanka ka fita fes ni ka barni a gida da katon ciki Kai ka gama aikinka shike nan,bazai yuwu ba ayi min ciki a dinga wulakantani an gama Dani an lalatani,Spark Yana kallonta yace ai na daina fada Dake ni tunda kika cijeni rannan,idonki ya rufe kika manta nine kika cijeni sai da kika fasa min fata a ranar na tabbatar wannan yaron na cikinki ya haukata ki,ni wannan yaron ban San irinsa ba,Almajiranta zan kaishi can,Kin fasa min mudubi Baki bani hakuri ba,tsokanarta yayi,hakurin me zan baka kana da kudi ka siyo wani mana ai dama kace zaka canja furniture,ni din nace zan canja furniture? yaushe? ni nace to,ai ka canja min kafin na haihu,zo ka zauna a nan na jingina,Spark idan baiyi ba dama yasan ba son sex take ba yanzu ya shiga uku baza ta yarda ba" Bata Jin Tausayinsa yanzu,bayanta ya Koma ya zauna tana tsakanin cinyoyinsa ta Dora bayanta a kirjinsa ta mimmike kafa a Saman kujera,tire din Yana Saman cinyarta,tace yawwa ko kaifa amma kawai sai dai ka fita,da ka fita mana na Gani,yace ni na Isa Yana dariya, ai ni gaba ta kaini Baby ki dinga sani Ina miki haka kullum,rigarta ya dage ya shigar da hannunsa ya shafa Dan cikin kamar ta fara ajiye tumbi haka yake,yace bari na fara branch a wajen Baby, sai yayi sama da hannayensa ya koma kirjinta,Naila tace ai dama baka kaunar Dan nan ba ta tashi kake ba,Spark yace Nima ba kauna ta yake ba,tunda aka same shi yake takura min tun Ina sonsa har na gaji,dariya tayi yace yanzu yau da na biye Miki da yanzu munyi fada yafi sau goma a gidan nan,na fasa mudubi kayi hakuri ai akwai kudi ka siyo wani,yace ai kayanki ne Dan mutum ya fasa abinsa ai ba damuwa,yanzu tunanin da nake ko zan samu irinsu a canja mudubin, Naila tace to ka bincika dai barna dai danka ne yayi ba ni ba,da Yana ciki yaushe ya fito yayi barna. Suna hira Yana Murza Naila a nutse,tun bata so bata ji sosai har ta fara shiga Mood,hannayenta ta goge da tissue tace bari na wanke hannuna,tunda yaji haka yasan yayi nasara. Hannayenta ta wanke da bakinta ta dawo ta furta Allah yasa bana karnin kifi,yace ai kece da ba ruwanki da kifi amma yanzu kullum ne sai kinci abinki,tace to ya zanyi Ina so.....bakinta ya rufe mata da nasa ya shiga tsotsa sai kace mayu duk kayan jikinsa sun tashi daga aiki sunyi mutsu mutsu,sun Dade suna Abu daya kafin ya samu shiga hanyarsa ya dinga kwasar gara a Palo, samu nutsuwa hirarsu suka dora cike da nishadi. Mero bayan tayi Sallar Isha a zaune a Saman bed, kwanciya tayi Haneef Ya sa ta a gaba Yana danna wayarsa sai da ya gaji tace baza ka kwanta ba? Kinga gado ne? ba gado,Mero tace oh gashi mu ba arna ba bare na matsa Maka ya kenan,dariya yayi ba tare da ya kalleta ba, har bacci ya kwashe ta Yana zaune,gajiya yayi da zama kafafunsa sunyi tsami,gashi bazai iya kwanciya a kasa ba shi,ta juya baya ya matsar da ita gefe can karshe ga gado Dan karami,Mero farkawa tayi kadan tace tace wash ciwona....sorry ya furta ya tsaya Yana kallonta,sai da ta koma bacci sannan ya kwanta a haka a bed din kowannensu kamar zai fado kasa. Juyowa Mero tayi da kyar taji ko Ina ba waje da kyar ma ta juya a Jikin mutum,idonta ta bude a hankali ta ganshi suna facing juna,murmushi tayi ta zubawa kyakyawar fuskarsa Idanuwa tana kallonsa sai da ta kalle shi son ranta tace yau Ina morewa,Dan ubanki Ihsan dawo ki sake fasa min Kasusuwa na,yatsa ta saka ta taba hancinsa ta cire hannunta da sauri,duk abinda take ba bacci yake ba Yana jinta,Mero tace fuskar gata da Dan fadinta ya kaga an Mari Haneef, marin ta gwada kamar zata sharara Masa Mari ta fasa,tace bari Muji gashin da Laushi ko karza ne ta shafa tare da lumshe Ido tace ba banza ba Yan mata suke kwarewa,idonsa ya bude da sauri Mero ta rufe nata tayi baccin karya. Yana sani yanda zata ji yace yawwa tayi bacci,Mero da sauri ta dunkule waje daya tare da boye kirjinta wuyanta ya taba ba shiri ta bude idonta,murmushi suka sakarwa juna a haka suna kallon juna ta juya Masa baya tare da furta sai da safe,yace good night. Washe gari Kwanan Mero daya a asibiti kawai sai ga Ihsan ta zo asibitin da kanta ganin Haneef bai kwana a gida ba,sanda ta zo ya fita siyo magani tana zuwa ta Kalli Mero a kwance Saman bed,Mero Ido ta bude yaga Ihsan ranta a hade,Ihsan tace Shegiya tsinanniya wato a Nan ya tare ya kwana a wajenki shine me jinyarki to bari na Kara rugurguza ki sai ya zauna jinyar da hujja tazo ta kama wajen da aka gyarawa Mero ta murde da hannu,Ihu Mero ta dinga tsalawa a asibiti,Ihsan ta kama Daya kafar ma ta dinga wujijjigata kamar zata cirewa Khadija kafar,Allah sarki Khadija kamar zata suma" da gudu ma'aikatan suka shugo suna rike Ihsan tare da kokarin banbare kafar Khadija a hannun Ihsan,Haneef ya dawo yaga abinda ke faruwa,Yana zuwa ya dinga zubawa Ihsan Mari har bai San iyakar su ba,amma Ihsan tace wlh ba Inda zani sai naga bayanta,Ma'aikatan ya sallama ya damki wuyan Ihsan ta fara kakari idonta ya firfito,Khadija tana kuka ta sheke da dariya me sauti taci gaba da kukanta ta sake fashewa da dariya taga ana Chaskara Ihsan,ya hadata da bango,tana Nishi tana furta a taimako,a....a...Taimaka min...Khadija Taga wani Likita ya shugo dan lukuti tace koma idan maganine na sha ciki kamar an Kifa kwarya,Likita ya rike Haneef dake faman caskara Ihsan yace mace ce fa ka shaketa tana kakari haba Sir, ya nuna Khadija yace wlh ba haka ake kishi ba,kina kallo abokiyar zamanki zai mata illa amma kiyi kuka kiyi dariya abinda kike kenan wato murna kike? Khadija tace ae murna nake ni kasan me tayi min,miji take aure shi nake aure matsayinmu Daya. Ihsan tana hakki taci wahala fuskarta duk ta Sha Mari ta tasa tace wlh sai ka sake ni Allah ya kiyaye nayi kishi da wannan kazamar,nafi karfin zama da ita ni dama nayi saurayina ka sake ni kawai,Haneef tsaki ya ja yace ke ai mahaukaciya ce baki San me kike ba me za ayi da mace me halinki,Ihsan tace ba Inda zanje sai ka sake ni wlh ta zaro wayarta ta kira Hajji da Maman Haneef tana kuka ta fada musu ku sa danku ya sake ni na gaji da fasikancin da yake da zinace zinace,Karuwa har gida bazan iya ba,Hankalin Mama ya tashi ta zaci da gaske ne tace kiyi hakuri Ihsan gobe zanzo Inshaallah,ni ba ruwana kawai ya sake ni ya auri wacce yake so ni dama na samu wani,Mama tace a'a ban gane kin samu wani ba,da aurenki yaushe kika samu wani? Nidai a fada Masa ya sake ni auren zumunci ne ban yi na fasa kowa ya zauna da Wanda yake so tana fadar haka ta kashe wayarta. Fitowa tayi asibitin tana sharbar kuka da kururuwa azo a taimake ni mijina ya kawo karuwarsa asibiti,Mutane da Yan zaman jinya aka taru aka cika, Ihsan tana musu bayani Yar aiki ya kawo min gida Ashe karuwarsa ce sun dade da sanin juna,bayin Allah ashe a boye dakinta yake kwana,da rana idan na tafi wajen aiki suna tare suna sabon Allah,tun suna yi a boye ya fito da shi fili,Ina zaune Yar aiki da ita yake Hira,da Yar aiki yake kallon film komai Yar aiki karshe har tayata girki yake a kitchen yanzu Bata da lafiya ya taho Yana jinyarta,ba iyayenta ba danginta babu mace shike jinya tare suke kwana ta ya bazan damu ba? Wata mace ta dafe kirjinta da hannaye tace wannan yayi asara,ai ni tuni na dawo daga safgar Maza,basu da hali tsaf zaiyi abinda yafi haka,wata ma tace amma wannan anyi matsiyaci,wasu kuwa suka ce sai hakuri mazan duk haka suke,Mace daya ce a ciki tace to ke duk kina me? Ya kamata a bincika maybe baya sonki ya aureki,ko Kuma kece bakya abinda ya dace har ya fada wannan safgar Allah dai ya kiyaye,mazan suna ji ba Wanda ya bawa Ihsan gaskiya a Maza sai ma cewa suka yi ke dai ba matar arziki bace ba matar rufin asiri bace,da matar arziki ce baza ki iya yiwa mijinki fallasa da tijara haka ba,mene birgewarki da cinyewa,wannan halin naki yasa yake kula wata,wani yace tab wannan bashi da mata ya Kara aure kawai,idan nine sakinta zanyi cewar wani,Ihsan motarta ta ja ta ware gida ranta fes ta fashe haushinta. Khadija da Haneef suna Jin abinda Ihsan tace da mutane,Khadija tace karka ji komai duk Wanda yayi Maka kallon banza kayi min kiss a gabansa ko uban waye na yarje Maka,dariya Haneef yayi yace banyi niyyar dariya ba fa Ina bacin rai,oh to ci gaba ke dariya koma ta furta, karka saki Ihsan Dan Allah,Haneef ya Kalli Khadija tare da sa hannunsa cikin nata yace zaki aure ni? mamaki tayi Jin abinda ya fada ba zato,tace Ina Yar aiki kalleni fa Ina ni Ina Kai me kudi, answer me" zaki aure ni? tafin hannaye tasa tare da rufe fuskarta ta furta ae,murna yayi yace na gode,su Hajji da dangina zasu iya hanawa indai ban saki Ihsan ba zasu ce bazan Kara aure ba,zanje da wasu da abokaina a daura mana aure ko basu sani ba indai Mama ta sani shike nan,ita nasan zata amince,Mero taji tayi nasara sai murna take a ranta. Arham daga kwanciyarsa Haly ta kira Mima a waya ta fada mata, Mima tana dakin Papa tace kaga ka samu Arham da kanka kayi Masa magana wlh tun kafin a Kai yarinya ko ayi mata ma gyaran Jikin yaje ya nace mata,gaskiya in baza ka Masa magana ba a basu gidansu su tafi kawai yafi,ai ba tsari kowa yasan me ake yi,Papa yace Inshaallah wani satin za a kaita ku fara shiryata,ai kafin wani satin ya gama da ita kaje ka yi Masa magana da kanka tunda mu ya Raina mu,Papa yace muje suka fito da Mima dakin Basma Muryar Papa suka ji Yana magana Kai Arham zo Ina nemanka yanzu a part dina,Yana fadar haka ya juya suka tafi,Basma tace kaje za a Maka fada,Arham yace ni Banga amfanin wannan aure ba,na kasa gane kan wannan aure,Basma tace asiri aka yiwa su Papa da su Mima, mahassada sun mana asiri,Arham ya furta naga alama Rafeeq ne yayi min asiri naga yafi kowa bakin ciki Dani sabo da nine sakonsa kar na kamo shi,Basma tace ko Kuma Kawuna ba kana gani Sadakin nan da kyar ya bada su,Arham ya furta ba abinda bazai iya ba sabo da yaga matarsa ta tsufa nononta ya zube yayi yaushi shine yake min bakin ciki,Basma tace Kai wlh da sauranta yarinya fa ya sake aure daga baya sabo da hadama,Papa ne yayi tsawa Arham baka ji ne,Basma itama ba wasa tace gashi nan dama wayarsa ya manta Papa ta furta kamar Soja mace,Arham ya gama saka kayansa ko wandon nasa bai kulle Zip ba kamar zai fado boxers a waje ya fito,Papa kamar ya fashe da kuka sabo da rashin kunyar Arham ta gallabe shi,kallo Daya ya Masa bai sake ba,yace muje marar mutunci,dariya Arham yayi,Papa yace kace baka sonta bata da kyau ban iya zabe ba,Papa subutar baki ce na gane gaskiya,idonka Yana Gani Allah ya saka da Alkhairi Allah yasa a Kara Maka matsayi a wajen aiki,komai yayi perfect,Papa yace kar na sake ganinka a dakin Basma ko tazo dakinka Kun rufe kofa,Kai baza ka bari a kaita ba,Baka sonta fa jikinta kake so wlh in na sake ganinka kaje dakinta ko tazo Kun rufe kofa zaka yi wani Abu sai na Saba Maka,in baka son albarka ka sake zuwa ku rufe kofa ko tazo ku rufe kofa,in kana son albarka Kuma ka kiyaye taba ta,duk wata mu'amula ban hanaka ba amma banda wannan safga,indai kana so in Maka baki dan Allah ka sake azo a fada min,Arham yace har da Baki,ai Allah ne yace Dokar Allah ne wannan,to shike nan kaje ka Kuma tafi ka bani waje,Arham ya juya ya tafi Yana mamaki yace a daura ma aure ace kar kula matar ni na taba Jin haka,shike nan zanyi biyayya. Komawa yayi wajen Basma ya bar kofar a bude,Basma tace ya barka ne? Arham yace yace yayi min Baki in na sake tabaki sannan kar na rufe kofa in muna tare sai an kaiki gidana,Basma tace har da baki? Arham yace kwarai,tace tab asiri ne,Allah ya karya shi ko waye cewar Arham,yace sabo da bakin ciki a aure ma sai an jefi mutum sai da safe ya juya ya fita,Basma ta rako shi bakin kofa tace Good Night bye ya wuce. Yana komawa a Palo ya samu Shaheed,yace Mazaje ya aka yi ne? Arham yace uhm Papa ne yayi min baki kar na sake taba Amarya,Shaheed yace illar zama gida Daya da iyaye kenan,Basma tana ganin rayuwa zama da sirikai,Arham yace duk Maman Rafeeq ce take wannan zigar,ka kiyayi matar data kashe aurenta ta dawo,ana tausayinta ashe ita bata Tausayin kanta,Allah ya kawo mata bazawari ko irin Baseeru Kusa ne cewar Shaheed,Junior Yana jinsu yace gaskiya Papa bai kyauta ba a nan ya dace ace ya bari ka dan more,Arham yace kaima dai ka fada ni basu gane nufi na ba ma bazan yi sex da ita ba wannan in ta dinga kuka ai sai kowa ya sani Dan Tabesting a hana mutum wlh duk Wanda naji ya kirani Ango a gidan nan sai na taka Masa birki ni ba Ango bane,Arham ya zauna yana ta surutunsa kamar me. Bangaren Basma kuwa kwanciya tayi abinta tana tunanin Arham dinta tace mutum Yana son Mijinsa a hanashi sakewa. Washe gari Misam yazo gidan Mima Yana gidan Rafeeq yazo shima Spark ya shugo suna zaune suna hira da Maman Rafeeq"Arham ne ya fito Yana Jin Haushin kowa Yana Bata rai,Misam yace Ango Ango ka Sha Mai,Arham yace duk Wanda yasan yayi min asiri yaje ya karya abinsa tun kafin ya dawo kansa Yana magana Yana kallon Rafeeq,Papa sun min aure an hanani taba Amarya,sai kulla min tuggu ake yi a gidan Nan Kuma bakin da suke gidan nan ne suke wannan hadin,Maman Rafeeq tace ni kenan? tunda nice bakuwa a gidan nan,Arham yace Nidai ban kama suna ba Baki nace karki fadawa yayarki tazo ta tsine min,Rafeeq yace baka da hankali ka zare Arham,ni dai ba ni nayi Maka aure ba... Basma ce ta fito sanye cikin doguwar riga fitted tayi kyau sosai,Arham ya bita da kallo Yana cewa Allah ya Kai damo ga harawa ranar kawai ku taho daukan patient zuwa asibiti,Basma ta karaso ta gaida su suka Amsa, Arham dake tsaye ta dan kalle shi ta rike hannunsa ta saki ta wuce, Maman Rafeeq tace nidai bari na tashi daga nan bazan iya Jin wannan Abu ba,Arham yace wlh yanzu na fara batsa a gidan man kowa ya gyara kunnensa ko a bani matata ko aji zancen Hallare da bado,haka kawai ba dama na kebe da iyalina na,Arham yayi Iyali inji Spark Yana dariya,Arham ya bi Basma,Misam yace Dan iskan yaro Hallare ta motsa Kai na tsorata da yaron nan Spark ya gado,Spark yace Kai baka ga iskancinka ba sai ni zaka ce ni ya gado Rafeeq ya gado,Rafeeq yace kwarai ni haka nake lafiya ce,inyi In Kara in sake yi bana gajiya haka nake,ni da naga Ikhram ma ba zaman lafiya,Spark yace tab sai kace Mima ya Kalli kofa yace kar ta jini suna dariya,Misam yace Allah yasa ta jika wlh yanzu Mima ta musulunta fada take yiwa yaranta. Arham Yana shiga kitchen wajen Basma ya samu Mima a ciki,Mima ya kalla ya Harare shi tace Ina Nan to,yace dan Allah Mima magana zan mata,ba ruwanka da ita na fada maka ayi mutum kamar ayu wai meke damunka ne,Arham yace gado masifa ne musamman irin na kaka Zeenatu,Basma tana jinsu tace Ina so in kulaka Sunshine to kar Baki ya bika na hakura ya jiya din?Dan kadan me Albarka cewar Arham,Mima ta dakko ludayi ta biyo shi da gudu,tana dawowa wajen Basma tace ke ana so a kwato miki yanci kafin a kaiki ya fara sonki na gaskiya kina shirme,Yana nunawa jikinki yake so ke Baki fahimta,Basma tace ai duk cikin so ne a so Jikin mace ma ai so ne yanzu idan wata ce bazai taba ta ba,ni kuwa nayi Masa na birge shi,ai kune da Kun San haka Mima sai ku bari kar a daura sai ya fara so na,kina biye Masa din Yana tabaki ba dole a daura ba,nidai tausayinsa nake ji gaskiya cewar Basama,jiya ma haka yace yace sirikai sun hanashi sakewa,kice dai sirikai sun hanaki sakewa,Dan Allah ki bamu hadin Kai Basma ya fara sonki da gaskiya,Basma tace abi ta shortcut Mima yafi,zaki ga Shortcut ki sake kulashi ki gani a gidan nan ana kwatar miki yanci bakya gani. Basma tayi shuru a ranta tace Ina naga wani yanci tunda aka yi min aure,a fili tace da dai an barshi ya karasa ragowar yancin dama babu ai Mima,Ina yanci ga macen aure,Mima Bata sake magana ba,tana kallo ta dakko sabon flask a kwali Shima zata farke,Mima tace wannan na Maman Rafeeq ne ta siyi abinta,ai bata da miji me zata yi da shi zan siya ya min kyau,Fisgewa Mima tayi ta Maida ta boye,Basma ta fito tana kuka indai ba a wannan flask ba to yau sai dai in Arham ya kwana da yunwa wlh baza ta Kai ba,Mima tace na Kai Masa da Kai na ta zuba Masa ta ba me aiki ta Kai,Arham yace Ina Basma fa kika kawo? tace baza ta kawo Maka ba sai a sabon flask,to a Bata sabon flask din mana bazan ci ba Nima a bata sabon tunda tana so,yanzu na kwace Sunan abokin Baban Naila Jauro bawan mata Nima na cancanci Sunan sai abinda mace tace wlh, Yar aiki ta koma ta fadawa Mima" tace ajiye a kitchen yunwa ai ba kanwata bace da kansa zaizo. Mima dai Papa ta samu tace Dan Allah tunda an gama komai a bar Arham su tafi gobe a Kai Basma haka sunfi karfina tun kafin ya fara danneta a gabana,Papa yace Allah ya kaimu ni kaina naga yau ko gaishe ni bai zo ba alamar fushi yake,kyale su a kaita haka ta gane kurenta a can, washe gari Papa ya kira Arham yace babu bikin da za ayi Arham zo ka dauki matarka ka bar min gida,an hada komai ku tafi,Arham yaji dadi kamar me yace ai yanzu Safiya ce sai yamma,Papa yace a'a ta ebo kayanta ga Lefenta suna wajen Mima ku dauka ku tafi,Arham yace da safe? Ae da safen fa ku tattara ku tafi karka Kara 30mnt a gidan nan,amma ai ba fushi kayi ba ko Papa? Ba fushi nayi ba Arham ai kasan fushina tunda ka matsu ku tafi ai ya fi,yace to mun gode ayi min nasiha,Papa yace a'a ai Kuna da hankali Kun fimu sanin ya kamata wacce nasiha,Arham yace ni ba a so na kowa an Masa nasiha ban da ni ,amma ai ita dai Basma din ayi mata nasiha ta kula dani sosai,Papa yace itama tana da hankali ai,ka karasa ladanka Papa in ka barmu haka sai muce fushi kayi, amma dai ko ayi hakuri da zaman tare ai kace. Basma da safe taji Mima tace tayi wanka ta shirya ta zabo mata sabon kaya cikin na lefe riga da skert na Leshi fari tace ki sa wannan,ta zaci unguwa zasu je ta shirya abinta sosai,Mima ta zauna dake ita uwa ce tayiwa Basma nasiha da fada na zaman aure,Basma tace wai ina zamu je ne? gidan miji za a kaiki,Basma a ranta tace sun ga haazaa,wa ya gaya muku barno gabas take,a fili tace tun yanzu za a kaini ai da yamma ake Kai Amarya,Mima tace ku yanzu za a kaiki shi zai tafi Dake daga baya zamu zo ganin gida,Basma tace to Allah ya kawo ku. Tana fitowa ta zauna a Palo ana ta Kai kayan Lefenta mota,Mufee suna zaune suka ce Basma kin dakko shanyarki kuwa? tace na manta na gaji ne ni an kusa kaini gidan mijina ma na huta da wahala,ga Inda zanje na huta na harde kafa daya kan daya" Nan kuwa duk an dameni ,Haly tace Allah ya taimaka Basma Allah ya baki hakuri Kuma,Papa yasa aka kira Masa Basma ya mata nasiha Shima a haka ma Mima ce ta dage sai anyi amma wlh yace bazai wa Arham ba,Ita Mima ta samu Danta tayi Masa nasiha,Arham sai da yaga an bashi matarsa sannan ya kwanta a cinyar Mima yace zanyi missing dinki yau Allah ya nuna zan koma Shan abincin yara,Shekara ashirin da Yan hayaniya da yayeni,Mima ta durma masa duka ya saki Kara,ni kake fadawa haka Dan ubanka? Kishi kike? Ke kika yayeni sai dai kiyi hakuri,Mima tace sai naji bana so ka tafi,Arham yayi dariya yace ya zama dole kuwa ai namiji Dan gidan wata ne,ya mace ake cewa Yar gidan wani ce inji Mima,yace Shima namijin haka Mima tunda ai dole ya bar gidan su,tace shike nan gobe kazo da wuri na ganka,to zanzo ai ko baki ce ba ma,za a kawo muku abinci? Arham yace Papa yace an hada komai na girki idan naga normal sai tayi in baza ta iya ba Kuma an samu matsala sai na kiraki a waya,amma na rana Dana dare kar a kawo da safe dai nasan za a iya samun matsala gobe da safe akwai matsala za a iya kawowa,tace to shike nan babban magidanci,dariya yayi yace kayana kadan na eba zan dawo na tafi da wasu gobe,tace to,yace Spark Yana cewa sai Nan da 4yrs za a Kara biki a gidan Nan to gashi matarsa ma bata haihu ba anyi wani,Kuma fa namu Albarka zaiyi ko ganga Daya ba a buga ba,ko kwano bai ce kwal ba bare a tara mata da Maza a gwamutse,Mima tace kar dai ka zauce,Dan Allah ka kula da yarinyar mutane,ka bi komai a hankali yace nine fa Mima Arham dinki guda karki ji komai. Arham ya shirya an fesa wanka na gaske kamar yau aka daura auren,Papa ya sa Driver ya kaisu,Arham yace to gobe na sa a kawo min motata,ba Wanda aka fadawa Kai Amarya daga Ango sai Amarya suka tafi. Amarya tana bayan mota tare da Angonta da hantsi gatsai gatsai. Maman Haneef washe gari tazo tare da Hajji da wasu Dattijai Maza dangi su biyu sun taho sulhu,Haneef Yana asibiti ,Khadija ta dingiso daga toilet tayi wanka ta fito ta zauna da kyar tana dafe bango,wayar Haneef ce tayi ringing,ya daga,Mama cikin fushi tace yazo gida suna Nan,sun samu Ihsan tayi girki ta kula dasu ta sake fada musu karya da gaskiya sun hau sun zauna,shi yasa cikin fushi tace yazo gida,Salamatu ya kira a waya tazo ta kula da Khadija sannan yace Khadija zanje naji,tace duk tsiya karka saketa Dan Allah tace ai tayi saurayi naga ta yanda zata auri saurayin nata mu gani,duk so take yanzu a sake ta sabo da ta samu Wanda zata iya juyawa son ranta,irinsu haka suke basa aure Dan soyayyar tsakani da Allah sai in zasu juya mutum son ransu sannan suke aurensa,ai yanzu taga baza ka juyu ba,karka saketa kace ka fasa auren in sun matsa daga baya sai suji a salansa,dariya yayi yace haka za ayi sai na dawo ya fice Salamatu tazo suna ta hira da Mero. Haidar sabo da ya samu kafar zuwa zance gidan su Mufee ya nace sai da aka daura auren Sudan da Rahma Maman Iman,ita kanta Iman sai labari taji,sannan Haidar ya dage wai biko zai Masa na Maman Rafeeq sabo da kawai ya fake da zuwa can,ana daura aure Jauro yace tunda miji a shirye yake itama in ta shirya za a iya sa rana su Habiba su rakata,tace Nan da sati zata tare,Iman sai labari taji ma,tace Allah Sanya Alkhairi. Haidar kamar uwarsa ce ta tare harda kiran Ikhram yace wani satin muna hanya zamu kawo Amarya,tace Allah ya kaimu,yace Ina yarinyar nan kuwa me hankali ta gidan su mijinki kanwar mijinki? Ikhram tace Mufee? Ai tana nan lfy,yace yarinyar nan Inda take birgeni akwai hankali ga ladabi,tayi a rayuwa Ina son mutum me hankali da nutsuwa,ga gaisuwa tana ganinka zata gaishe ka,Ikhram tana ta dariya a ranta tace bai san iskancin da suka tsula ba duniya ce ta bi da su,Ikhram taci gaba da zuga shi tace ai duk tafi matan gidan hankali,yace gata kyakyawa,tafiyarta kawai abar kallo ce wani chafe chaf chaf....zanzo ki jawo min ita,duk da Ina da number dinta amma kwarjini take min gashi tana ta ja min rai,haka nake son mace me aji...Ikhram tace ai indai kana ciki zan Maka campaign,yace Dan Allah ki taimakawa Dan gaba da fatiha,irinku sai an tsaya mana muke samun aure,tausayi ya bawa Ikhram tace a ranta Iyaye suna cutar yara irin wannan,mutum har mutum irin Yaya Haidar,tace Inshaallah Yaya Haidar kamar ta zama taka,su basu da matsala wuyarta na fadawa Spark wlh sai an baka,ko Rafeeq sai Inda karfinsa ya kare akan wani nawa ya samu ci gaba ba abinda bazai min ba,yace na gode sister Allah ya bar zumunci Mama ta kusa zuwa gari tace nan da sati inshaallah tare zamu zo Abuja,tace Allah ya kaimu dan Uwa" ya kashe wayar tare da furta Ameen. Masu Sharhi Wanda basa gajiya Ina matukar godiya. AsmaBaffa [2/28, 7:36 PM] AsmaBaffa: 🏫TANTIRIYA🏫 A GIDAN YARI BOOK 3 ~TAIMAKO~ 51-55 Official By AsmaBaffa SADAUKARWA NE GA AIDA MAMAN TASNIM Page naki ne Sailuba Abdullahi Sani *ZINARIYAR MACE⚡* *Wai shin 'yar'uwa menene matsalarki? zubewar nono, ko kuma rashin kwankwason juyawa a falo maigida ya shiririce ya manta da tibi da matan tictok, menene matsalarki ne? rashin ni'ima ko kuma mugun sanyin da ya yi miki katutu, shin rashin taushin fata ne ko kuma kuraje da tabbani, ko bala'in ramar da ta addabeki kuma babu rashin ci ba rashin sha a gidan auranki, gwaigwayewar gashi ce matsalarki ko kuma kaushi da faso na tafin kafa da bushewar fata, kina bukatar fatarki ta yi glowing kalarki ta fita kuraje su mutu, ko kuma kina bukatar azababbun turaruka da humra tare da turarukan wuta. Na san dai kuna da yawa matan da tumbi ya yi musu karan tsaye ina nufin ya katse muku hanzarin yi wa maigida gwalli da muskuce-muskuce a falo😃 Nesa fa ta zo kusa AL-KUTUBIYYA ISLAMIC MEDICINE sun tanadar muku da nau'in magungunan da suke magance kowace irin matsala da izinin Allah. Babban burinmu shine sha'ani na aure ya inganta a samu daidaito. Muna da.* Na gyaran nono. Na sanyi. Dilka tare da hadin sabulu. Duk Wani nau'in maganin mata. Humra turarukan wuta perfumes, original miski tahra 3in1, ciccibi budurwar kaza. Had'addun supplement irin wad'anda ba su da matsala. Maganin Sliming wato narka tumbi. Abubuwan da muke sayarwa suna da yawa, kuma babu asarar dukiya. Muna garin kano kuma muna tura kayanmu kowane gari fad'in Najeria da Nijar har ma da kasashemn ketare. Kai tsaye a tuntu'bemu ta lambobin wayarmu domin karin bayani. *08089965176* *07084653262* Arham suna mota ya Kalli Basma yace tunda nake ko a film banga biki irin namu ba sai kace a America ba kowa ba gata,Murmushi Basma tayi tace ko a jikina an tsikari kakkausa ni dama so nake na huta sai abinda naga dama,Arham yace abinda kika ga dama? abinda dai naga dama ai sai abinda nace,Basma tace na girki fa nake nufi da zaman gida,Arham yace sai abinda nake so zanci,sannan na baki uhm uhum hum ya rufe bakinsa yace bari nayi shuru sai lokaci yayi zai nuna,Basma tace na San me kake nufi fa,mu ba wani yare da za ayi mana bamu gane ba,hannun Basma ya riko Yana Murza yatsunta masu kyau,tace ko lalle babu,yace rabu da su zan kaiki ayi miki, wai ba gyaran Amaryar maganin Infection ne ba da na ni'ima ba? tace haka aka ce yace rabu da su zamu yi abinmu,idan naga dama sai nayi zuciya na fasa komai sai anyi gyaran,kyale su Mima haka ma za ayi,zan basu sample, I just wanna have fun to night amma zan iya hakura ko dan bakin cikin Maman Rafeeq so nake sai tayi kuka tunda bata son mu Arham ya furta. Gidansu me kyau Madaidaici Driver ya kaisu,gidan ya tsaru matukar gaske,Arham suna parking ba kowa a gidan shi da driver suka fito da kayan suka shigar da su sannan ya aiki driver ya fada musu Inda zai je ya siyo musu abinci lafiyayye,Basma sai murna take komai na gidan yayi mata an kashe mata kudi,Ango kuwa da kansa duka akwatuna goma cif ya Kai mata bedroom dinta ya kwashe nasa ya Kai nasa dakin,sannan ya dawo Palo ya gwada tv da komai normal,kitchen ya shiga ya jona su gas duk an hada,ya duba Store tare da kiran Basma da ke aikin kalle kalle yace duba ki gani komai yayi ko akwai abinda kike bukata,Basma harda iyayi tace akwai wani curry kala uku da nake bukata,yace sai gobe sai a kawo Yana kare mata kallo Yana murmushi Yana tauna chewgum,Basma tace yi poster a haka kayi kyau,ya tsaya kuwa a haka Yana tauna chewgum din sama sama, tana murmushi tace kamar dan bariki ni dama haka nake son miji,da Papa talaka ne wlh sai ka Shekare baka yi aure ba,Allah ya taimakeka dai,yanzu ma rashin kunyata ta jawo aka yi min,ki duba gidanki ki gani idan da abin gyarawa naga dai ko mai neat ne,tace sai kayana zana shirya,muje to mu shirya,suna zuwa suka bude kayan lefe suka hau shiryawa suna fito da na fitowa,Arham ya ciro wasu material English gown yace ga wannan zaki saka? in kana so mana,duk abinda nake so shine a Lefen nan,Basma tace tab masu karamin karfi Kun shige su baza ku samu kwancen kayana ba mijina ya naso,dariya ta sake yi tace Allah abin dariya kusan fa mate Dina nane Kai da kadan ka girme ni,yace Kuma a haka zan baki kuka ba,ki rufawa kanki asiri abinda nayi niyya ya tabbata zan fasa wlh nayi maganinki yanzu gashi mu Allah ya hore mana Hallare tabarakalla mashaallah akanta sai kiyi yaji,dariya Basma tayi tace ku kuke da abu daya ai mu mata....Kinga wannan jambakin Ina sonsa a dinga shafa min Ina shanyewa,sai da suka gama shirya kayan tas sannan ya dawo kan inners ta zaba Shima ya zabi wasu,yace wannan bra din sunanta yi shurunka nono,dariya suka yi ta daga kafadarsa. Yini suka yi suna shirya gidansu Inda baiyi ba suka gyara komai,har kujerun ya kalla yace basu yi ba aba ta Kalli kofa ya juya ya canja mata position,gashi sunci sun koshi abinsu,Basma tace saura me gyaran jiki,yace karki damu za ayi,fes za a gyara min wajen zan bawa su Mima mamaki,Basma tace ai Gani suke mu yara ne suna kallon jikina wai kake so,Arham yace kyale su zasu ga yaro abokin tafiyar manya,Rafeeq ne ya kira shi da niyyar aikensa kana Ina Arham? Ina dakin me dakina,Rafeeq yace bana son wasa,yau fa aka Kai mu dakin aure ka tambayi Mima,to ai yanzu ba abinda kake yi,yace tab wallahi yanzu ko Papa ne bazan fita ba bare wani Yayana,sanda. nazo auren nawa me kuka bani Papa ne ya min komai sabo da haka ba Wanda zai aike ni naje ,Rafeeq yayi murmushi yace sabo da kayi Amarya? ai Amarya ba karya bace abinda kake yi shi zanyi nima,Basma ce tayi magana kaga wannan a dauke su? Yace ae sunyi" su zan saka da dare ko? Arham yace ahhh na tuna a canja su ba yanzu ba,Rafeeq yace ashe dai da gaske ne Arham,zauna wasa Rafeeq asirinka ya karye,dariya Arham yayi kawai ya kashe wayarsa. Spark ya kira yace wai kaji Arham ya tare yau? Spark yace na sani ni ai,yaron nan sai gori yake ba a bashi komai ba Kuma gaskiya bamu kyauta ba,Spark yace uban me zan Masa bayan gidan nasa ni na zuba musu komai na ciki,papa ya gama gini nayi kayan ciki bai sani bane rabu da shi yayi ta Jin haushin,Rafeeq yace wannan gorin na Arham bari na fadawa Misam mu tura Masa kudi,Misam ya kira ya fada Masa,Misam yayi dariya yace bamu kyauta ba gaskiya Nan take suka Masa transfer ta kudi na kirki,Arham Yana Gani yayi dariya yace sunji gori sun turo kudi,saura matan gidanmu masu aure su Anam. Basma tace sun baka kenan tana taba gashinsa,yace sun bayar sun wanke kansu saura Spark babban nasan Naila ce bata yi magana ba,amma tana cewa turawa Arham kudi zai bani,Basma tayi dariya tace nima haka zan koma,yace ai zaki iya tunda kina da abin bayarwa,kina da Bado sai dai yanzu ba a San kansa ba tukun. Basma tace ni nasan kan abina ai,murmushi yayi tare da furta an gama gyaran? tace ae an gama,yace to yanzu bari kiji ko Ikhram bazan kira ba akan gyaran Jikin akwai Babar abokina Yar Sudan ce me kyau take yi,ciki da waje zata gyara min ke,tace to ayi mata magana,a waya ya kira abokinsa yace Dan Allah hadani da Mama,yace to ya bata waya suka yi magana ta fada Masa abinda za a kashe,Nan take ya tura kudin tace a kawo ta yau. Sai da kowannen su yayi wanka Arham yace driver yazo ya kaisu unguwa,ba bata lokaci yazo suka je wajen me gyaran,a ranar ta fara yi mata ta bata wasu magungunan ta fara amfani da su sai skin da ta gyara mata ta taba wasu subulai da sauran su. Suna kan hanyar su ta komawa gida ya musu take away suka wuce gida. Maman Rafeeq suna zaune da Mima tace Basma yau zata yabawa Aya zakinta,Mima tace yanda Arham yake ai sai ta ji jiki Kinga bakin rashin kunya ya mutu an huta,gobe da wuri zan bawa su Haly abinci su Kai daga nan su gani lafiya take in tana bukatar agaji sai kije,Maman Rafeeq tace bazan je ba wannan marasa kunyar yaran naje na ganowa idona,in Baki je ba waye zai je to,shike nan Allah ya kaimu. Arham Shirin bacci suka yi cikin kayan bacci masu kyau,ya damu Basma mu kwanta,suna kwanciya kamar zata narke ashe Basma an iya kissa da shagwaba,bargo ya lulluba musu yace gida yaji rufi ga kwano ga ceiling duk sabo da kar a ganmu,Basma ta fara Masa shagwaba haka kawai,Arham yace Nidai na shiga uku da duniya yau din nan har an tafi da Imanina an gama Dani,bazanyi karko ba Yar Aljanna da wuri zaki mallake ni,gwara Spark Dani ashe,dariya Basma tayi tare da shigewa kirjinsa sosai tana wata sabuwar shagwabar,Arham yace na bar miki motata na dinga aronta a wajenki Ina fita,Basma tace a'a ni dai....ka rike watarana idan ka bunkasa da kudi sai ka siya min tawa kajiiiiiii.....ta karasa da wata shagwabar Arham yace Dole na bar miki ita sai kin karba ni Kuma sai na dinga aro Ina fita,Yana magana Yana cire mata rigar baccinta a hankali har ya zare ta,Arham ya furta abu haka mashaallah,Basma tace ai ko ni na Kalli jikina na gansu sai nace Allah na gode ma na fita kunyar mijina,Arham da sauri yace ahhh kin fita tass,ya shiga shafe su yana murje su Haneef gidansa ya shiga Mama tace sai yanzu kaga damar zuwa kana can wajen kanwar uwarka ko? Hajji yace abin naka Kuma yayi yawa fa,meke faruwa ne wai,Haneef ya zauna yace Ina Kwana Mama,karka Raina mana hankali rike gaisuwarka tukun,Ihsan tana ji ta fara hawaye da kuka tace ni na hakura da aurensa ya sallame ni kawai,Mama tace duk abinda kaji mace tace a sake ta to ba karamin abu bane,yanzu Haneef har ka Kai matsayin ajiye wata banza a gidanka? Yaushe ka lalace ban sani ba? Tarbiyyar da na baka kenan Haneef, rasa ma me zai ce yayi,Mama tace to tun muna sheda juna ni da Kai ka sallami Khadija ta koma gidan iyayenta ko Kuma ta koma wani gidan aiki" bazai yuwu ba. Haneef yace Mana bani da da laifi ni,lokacin da nazo muku da abinda take yi....kuka Ihsan ta saki ni ka sake ni na fada Maka,Nan take Haneef yace ya na sakeki saki daya dama ni kin isheni na gaji da rashin mutuncinki,kowa ya sheda nayi a gaban ku na saki matata saki daya,Ihsan ta saki kururuwa wallahi saki uku nake so sai kayi min saki uku idan uwarka ta haife ka da jini ka karasa min Sakina,Mama ta bude baki tace a gaban nawa? a gabanki ai ba uwata bace ke,Haneef yaji dadi da tayi a gaban su suka gani,tace duk ba kune munafukan ba sai da kuka gama waya da danku zaku zo nan Kuna mana wani kaza kaza,Haneef Yana ji yaki magana ta dinga cin mutuncinsu,Mama ta fashe da kuka ko yi shuru Haneef bai ce ba,yace ai ku kuka jawo Mama sai dai ayi hakuri Kuma. Ihsan ta mike ta shiga dakinta,duk da haka taji ciwon sakin matuka,Mama ta gama kukanta tace rayuwa ce idan da ranmu zamu Gani,Hajji yace Haneef kayi gaggawa ba a biyewa mace,Haneef yace ni biye mata zanyi wlh bazan dauki wannan ba,hakuri sai ku mutanen da Banda mu yanzu,akwai abinda ma Bai kamata kayi hakuri a kansa ba,matar da ko hakkina bata bani ai nayi rawar gani ma,in wani ne wlh tuni ya sallameta a iya case daya na Ihsan yaci ace na sake ta,bana sonta ni zuciyata wata take so,Mama tace ni Kuma baza ka auri Khadija ba idan ma sabo da ita kayi sakin,Haneef yace to ba damuwa gwara na zauna a Gwauro nasan a Gwauro nake yafi min mutunci,amma mace irin Ihsan me za ayi da ita kirjinta baza a taba ba duk da ba sonsa nake ba ai tayi min Kara tace gashi,shike nan ni a haka zan kare komai ace Yan uwa,zumunci dai zumunci bazan iya ba. Mama tace to na fada Maka Khadija ta San Inda dare yayi mata tunda zuwanta ba Alkhairi bane tasa ka rabu da matarka ta hada ku fada wannan ai shedaniya ce kawai,Ihsan tana daki tana waya da wani tace a samo mata gidan haya me kyau na gaske Kuma a GRA. Mama kwana zaku yi? Haneef ya tambaya? tace Allah ya kiyaye mu yanzu zamu tafi tunda a gaban magabata kayi saki mene amfanin mu,dariya Haneef yayi yace Allah ya tsare, sauran dattijan kuwa basu iya cewa kala ba sabo da Haneef Yana da kudi, fadan ma sai talaka ake iya yiwa shi. Kudi ya basu ya sallame su suka wuce shi Kuma ya kwanta bacci,Ihsan ta zaci baya Nan ba kowa ta fitar da kayanta ta siyo kanarzir zaka Kone Masa gida,ta shigo Palo da galon a hannunta sai gashi ya fito ya Sha shadda Sky Yana kamshi da alama fita zaiyi,tsoro taji ta fara kame kame,Galon din Dake hannunta ya kalla ya tako ya fisge tare da budewa ya gani hannunta dayan ya kalla yaga harda lighter,yace gidana zaki Kone zaki sa min gobara? juyawa tayi ta fice da gudu ta bude mota tare da zuba akwatunanta ta shiga ta fice daga gidan,Me gadi yayiwa Warning yace kar ka bari wannan yarinyar ta shugo min gida ko da wasa,idan na ganta watarana a nan a bakin aikinka. Bai koma asibiti ba Office yaje sai dare ya kira wayar Khadija yace kicewa Salamatu ta tafi gida yanzu zanzo,ko da ya Koma bai cewa Mero wani Abu ya faru ba yace kawai anyi settling komai,Mero taji haushi a ranta Dan me za ace ai anyi Settling dama Yana son Ihsan,tambaya ta sake yi tace kace anyi Settling? Komai an saita shi?wato komai ya saitu? Yace ae komai normal ki tayani murna ya rugume Mero tana daga zaune Yana gefenta,Mero tace a dinga tunawa mu dai Musulmi ne,sake kankameta yayi,Mero ta zaro ido tana Jin kamshinsa Wanda ya kashe mata jiki,kokarin ture shi take yace please ki dan tsaya,Mero ta tsaya tana cewa ban sa bra ba kana ta Jin bati,maganar da tayi ya sake Maida hankalinsa kamar zai Maida ta ciki Yana sakin ajiyar zuciya Jin ai bata ma da bra,hannu ya Kai zai taba boobs Mero ta boye jikinta da sauri ta zame tace ka bari a daura aure,halina da soyayya da Gwauro kenan,dariya yayi yace zaki bayani zaki ga Gwauro. Kwanan Mero biyar aka sallameta tana takawa normal kadan take dingishi,bayan sun koma gida Haneef bai San zata fita ba ta shirya ta tafi kasuwa,tunda tazo Bata taba yawo a cikin Kano ba baza ta iya Kai kanta gida ba idan ta Bata,ganin da waya tace in ta bata ma sai ta kira Haneef,sai da ta je ta gama siyo ganyen da zata yi girki da shi da Yan abubuwa tazo zata dawo gida ta rasa unguwar ko suna bata sani ba,waya ta dauka ta kira Haneef yafi sau ashirin bai daga ba,Mero ta rasa Ina zata je tana ta tafiya a kasa kamar tayi kuka,Motar Jauro ce tayi Slow a wajen shi da Abba,Abba Dolo yace ga wata yarinya da alama Yar unguwar ce mu tambayeta tunda ni naga ba mutane a nan haka,Jauro yace kar fa ta zanci sonta muke,Yo sai dai Kai ni Ina da Yar Inna Allah ya bawa me rabo sa'a ya samu wannan halitta ta Allah ya more rayuwarsa,Jauro yace Kai ana haifar mata da kyau yanzu ba irin zamanin mu ba,da fa Gani nake kaf garin mu babu me kyawun Habiba ashe hauka nake,Abba yace a'a Jauro dama kasan da irin su Kubra Yar Inna duk gasu Nan,ga Ade ma ga Hajara me Jan lebe,ga Bingel me idon Madara duk a lokacin sune mata masu ji da kyau musamman Kubra tawa,oh su Kubra anyi farin jini an more,layi ake kafawa sai ta kare a Hashimu Dolo,Jauro yace ai Kai naka shine me kyau na wani banza ne a haka nake son matata Habiba Glass ya sauke yace da Mero da Allah yarinya tambaya muke, Mero ta daure fuska ta juyo a yangance tace Malam kayi hakuri bazan taba soyayya da Kai ba,bana son wani da namiji baka ganni ba kalar Instagram? Ko baka ga nayi kala da Twitter ba? Dan Allah ka nemi wata ni bana sonka,wait wait wai waye yayi magana soyayya ana daga magana kin San uzuri....bazan taba sonka ba koma mene bana soyayya ni,wa yake zancen soyayya cewar Jauro,dama haka kuke Dattijai da Kunga kyakyawar mace me aji sai kuce Kuna sonta,Jauro baki ya bude kawai,Abba Dolo ne ya juya yace Nima wlh Allah ya isa da kallo na da kika yi da matata da komai da girmana da yarana sabo da Allah yayi min baiwa ta kirar matashi,kin ganni kamar saurayi shine kike kallona bazan taba sonki ba Allah ya kiyaye min,ke ni a namiji ma nake kallon ki shi yasa ma muka tareki zamu yi tambayar,Mero tace ai daga tambayar sai ace an gode sai karbar number bada ni ba ku nemi wata ta juya ta tafi abinta. Abba yace ka gani ko wannan da bata fi sa'ar Naila ba ko,yanzu wannan idan Naila tana kusa tayi mana haka ba sai ta kusa nakasa ta ba,Jauro yace bare yarana su Haidar, Abba yace duk da haka fa ta cinye mu a wasa yi gaba ka sake tareta sai na rama,Jauro ya ja mota tare da tsayawa a saitin Mero Inda take tafiya,tsayawa ta sake yi tace Dan Allah Ina ganin girman ku mana ku kyale ni,babbar yarinya ce ni kalar celebrities ce ni,Abba yace ke rufe mana baki ke baki ji kunya ba,kalleki wai kalar Cele, ya kike dakko abinda yafi karfin ki kina likawa kanki,kika zama Cele ai sai an rufe ma'aikatar idan film kika shiga sai dai a rufe Industry baki Daya domin babu me kallon ki, Instagram Kuma da kike ta cewa ke kalarta ce da me Instagram zai ganki da idonsa sai ya tsinewa kansa da ya bude Instagram,ke da ya San ma kina shiga shafin sai ya fashe da kuka,Dariya Mero tayi tace Dan baka ga Wanda zan aura bane,wlh in kana magana sai na ga kamar wata Naila da na sani amma ita a Abuja take,wlh Kuna yanayi,Abba yace 'yata ce ma tana da miji Spark? Mero tace wlh itace nan,Ina da number dinsa bari na kira shi,Abba ya Bata rai yace kar dai ki sake naji labarin za a karawa 'yata kishiya ace kece sai kin daidaice a duniya,Mero tace nima Ina da nawa Baba wannan ni bazan kishi da ita ba jarabarta ta fita karfi,Abba ya washe baki yace haka nake so taci gaba yi. Mero ta kira Spark bugu biyu ya dauka yace Mero ya aka yi? tace Ina yini yace lafiya Alhmdllh,dama Baban Naila na gani gashi naga suna kama yace ai babanta ne,Spark yace talla kike yi a birni da kuka hadu da Abba? Wanne Talla naci gaba na zama budurwar me kudi,ai shi yasa kaji ko neman ku bana yi sai da dalili sai ko a gaisa,amma da ace ban samu madafa ba ai dawowa zanyi a hadani da ko Arham ne nayi manage ko yaron nan Shaheed me kunnuwa,Spark yayi dariya yace to bawa Abba wayar,ta mika Masa ya karba suka gaisa sai Spark ne ya fada Masa dalilin zuwan Mero gidan Mummy,Abba yace Allah sarki Ashe Yar aiki ce ma Kai duniya ta cika da Yan karya,cewa tayi Kalar celebrities ce ita,kalar Instagram,ita fitacciya ce,Abba har da cewa ka dinga takatsantsan da kula mata marasa aure suna haifar da tarzoma a gidajen masu aure,ka kame kanka da taimakon Yan mata wasu daga taimako zasu taimakeka ato,a dinga Jin tsoron Allah kuma a kula da iyali sosai a kyautata musu,su Iyali ba abin wasa bane,ko waya kayi da wata ka fada ma Iyali sabo da gudun zargi,Spark dariya kamar ta halakashi haka ya danne yasan sabo da Nailansa yake fadar haka suka gama waya,Jauro ma dariya yayi yace wato Kai Yarka kawai ka sani,Abba yace so so ne amma son Kai yafi ai,Abba yace ke a layin nan kin San gidan Isyaku me shanu? Mero tace nima bakuwar ce Bata nayi na rasa gane gidan da nake,na kira waya ba a daga ba,Jauro yace Amma kika bata mana lokaci ya ja motarsa ya bar Mero a Nan a tsaye kamar Soja. Wayar Haneef ta sake kira ya daga yace Ina meeting kafin tayi magana ya kashe,Waje Mero ta nema ta zauna tare da zuba tagumi,sai yamma likis tun 11:30am ya kirata a waya ta fashe da kuka,rikicewa yayi Yana tambayarta mene ne? tace fita nayi na bace a hanya tun 9am na fita,na kira kaki dagawa na zauna na yini a a hanya kumaaa.....ta karasa da kuka,yace sai ki min text kema,kina Ina yanzu? Ni ban San Inda nake ba Ina dai kusa da wata transformer wlh zan rungume ta,sai na rungumi transformer, kina ji na shiga napep ki bawa me napep wayar,tace to tana goge hawayenta,Napep ta tare ta mika Masa waya,Me Napep ya Fadi Inda take sannan ya Masa kwatancen Inda gidan yake,ya tafi kai Mero gidan suna shiga layinsu tace na gane ga gidan can,suna karasawa Haneef ya fito daga gidansa ya sallami me napep ta zo wajensa,yace gashi nan ana gani an San kin Sha wahala,Hannunta ya rike suka shiga ciki,me gadi ya zaro ido ganin Haneef ya rike hannun Khadija,Iro yace dole Hajiya ta gudu ta bar ladanta. Haneef yace gobe ki shirya zan kaiki gidanku,tace to Allah ya kaimu wai Ina Aunty ne bana ganinta? ta koma Adamawa tana can,ta samawa kanta lafiya Dan wannan gidan na Amarya ne ita kadai,duk da haka ai zaka kaini Adamawa din sai naje can ma mun fafata da ita cewar Mero,so kike ta sake karairaya ki kenan,tace ai zata gane kurenta ne hmm... Arham ne ya shafa mazaunan Basma yace gaki da shugaba,Basma tace Allah ya nufa,ke baza ki min komai ba? Kunya taji tace ni me zan Maka ai ko harararka bazan yi ba duk abinda zaka yi,yace ba wannan ba dadin fa da zaki sa naji? Basma tace wayyoooo nikam na shigesu aikin mitsitsika Hallare ya same ni na shiga uku nidai ko ta yaro bana ganinta nauyi take min a Ido,kika ce ni yaro ne? Ni da nake yaro,Allah ka wuce yaro sau nawa Ina Jin sawunta a jikina ta furta a zuciyarta Kuma tace ko Papa bazai ja da Kai ba,tasa ma yanzu ta fara komawa baya sabo da tsufa,Mima ana maleji a cikin mota mu kuwa muna zaune Saman lafiyayyar kujera Hallare ta yaro matashi za a Dade ana cin Duniya da tsinke za a Sha gwagwarmaya da ita,Arham yace me kike cewa ne? cewa nayi zan Maka ko me kace,tace to zan na koya miki,tace mitsikar? dariya yayi yace wannan hausar taki sai garinku mene wani mitsika,dukkansu sai guntun wando a jikinsu Labbanta yake kallo anutse yace muga bakin? dagowa tayi ta bude a hankali ya shigar da nasa cikin nata,murmushi tayi ta duke shi a kirji,tana so ta yi magana ba dama Yana ta faman aika mata da sako Yana tsotsar bakinta hannayensa na aiki a Saman kirjinta,Basma sai Kara shigewa jikinsa take Nan take duk ta zama wet,tace Sanyi ya kamani Abu Yana ta fitowa,Arham yayi dariya bazai iya magana ba sai murmushin kawai,Basma ma ta shiga yanayi tun ba aje ko Ina ba,Arham da kyar Murya na rawa yace bazan iya jira ayi gyaran Amarya ba ni,na fasa,dadi ya kwashi Basma tace dama Kaine kace ni banga amfanin Hakan ba,ance da zafi wlh amma ni ayi kawai nayi kuka na kawai na wuce wajen yafi min,tunda kawayena sunce akwai mugun zafi Kuma sai anyi kuka, Dan wandon ma ya cire,Basma ta Kalli Hallare tace angaida Malam jazuli Sunan wani makwafcin mu,a ranta tace uhm Allah yasa ba zafi sai kukan da zanyi kawai ance sai anyi kuka. Sai tayi ta mimimi da baki in bata so yaji maganar, kunnenta ya shiga hurawa iska a hankali yana sa harshe kadan,Basma ta lumshe ido tace Ina kasan duniya ne haka? dariya yayi yace ba yanzu zaki San nasan duniya ba tukun sai nan gaba,bakinta ya Dora a nipples dinsa yace duk abinda kika ga dama kiyi,Basma tace kar a dinga jansa ya fito nono a kirjin namiji babu lafiya,ba abinda zanyi halittar mu daban taku daban,tace to ta fara jiyar da shi dadi Yana Sambatu Yana kukan dadi, tana zuwa kan Hallare ya susuce,harda cewa ba a taba yi min ba kiyi min karki dauki hakkina,Basma tace abin har ya Kai ga daukan hakki daga abin arziki shine zaka ce zan dauki hakkinka tun yanzu zaka fara hadani da Allah jeka da hallarenka na fasa,wayyo yi hakuri wallahi ba haka nake nufi Dan darajar tsohonki ki yafe min my Sunshine,My Currency,kudi fa kenan nice kudinka? Yace ae mana to Allah gobe sai ka kaini shago kayi siyayya da ni a baka canji,ya dinga lallaba Basma Yana sata abubuwa masu nauyi,tana fara Masa sucking ya rude ya dawo kamar ba Arham ba,sai da Basma ta firgita,tsoro ya bata duk abinda yace sai tayi sabo da ya gama tsorata ta,taji kamar ya haukace irin maganganun da yake zubawa,da Nishin dadin da yake yi,ga jikinsa yanda yake mazari,sarrafata yake ta ko Ina,a hankali da salo yasa ta bude Masa Bado ya gama sarrafa shi da baki, Basma ita ma ta susuce masa da ihu har da cewa kayi min me zafin nayi kuka na ni na huta tana shagwaba cike da shaukin kauna, dama kadan yake jira ya fara neman hanya,tun ba ayi Nisa ba ta bare baki,tace zafi nake ji,na fara Jin zafi, wajen zai yage fa ta fara kokarin guduwa zata kwace kanta,Arham a haukace yake bai ma San me yake ba shi ga tarin kuruciya,kokawa suka fara yafi karfinta tuni ko motsi ta kasa ya jigatar da ita da kokawa ta hakura,lokacin ya kutsa ciki,Basma Sunan babarta Wanda Yan gari ke fada mata shi ta dinga kira tana cewa Magajiya me goro.....Magajiya.....Me goro.... Magajiya.....wayyoooo zan mutu,Ashhadu Allah ila ha illallah wa anna muhammadurrasulilla(SAW) ashe ba yaro bane wlh da shekarunsa... Ta dawo Mima...Miiiiiiiima......danku zai kashe mastarsa,kuzo ku yiwa danku fada,Ashe ba iya kuka ake ba zafin ne na jaraba...shi kuwa Arham Sambatu yake kawai Yana kukan dadi yace motar nan dole sai kin karbe ta na dinga aro,Basma tace ba a so baza a karba ba,Dake a zauce yake harda rokonta pleaseeee.....kudina na account du na baki gwara na zauna a talauci na.....Abu dai tun Basma na kuka da magana cikin sauki har ta dawo na fitar hayyaci,matsalar sanda aka kawota suka zo gidan duk garin taba mata jiki ya rage zafi ya kawo bata sani ba,shi yasa yanzu Kam ya dade,sai da ya gama facaccala Basma har ta daina iya magana sai kuka kawai Shima ba sauti sai hawale,gata Nan ba wani jini ne ya fito ba sai raunin da ya ji mata ya wuce tunani,kuruciya yayi kawai gashi bai taba yi ba,shi kansa a gefe ya bingire ya hada uban gumi,Yana so ma ya karo karfin AC din amma Ina ya kasa bashi da karfi ko kadan,yace wayyo gwiwoyina a bani ruwan gishiri Dana sugar ko sa mike,a bani glucose na Sha,ya kwanta yayi rasha rasha itama haka ba Wanda yake magana sai kukan wahala,ga Arham da kwailo,hannayensa ya mika Yana tattabawa har ya tabo Basma yace sannu kinji,wai kuwa munyi addua ma? Basma ko magana taki yi wai tayi zuciya tunda tayi ta kuka tana roko ayi hakuri haka a kyaleta anki to tayi zuciya baza ta sake magana ba. Arham yace Ashe dadin ma da wuya ake cinsa gwiwata sai tayi tabo,Sunshine ya naki ai ke sai dai Bado Ina Jin sanda na keta shi gida biyu,shike nan sai anje asibiti maybe,Basma taji Tausayin kanta ta fashe da kuka tace ai sai da nace ka daina kaki ji har Magajiya me goro na kira ai ko darajar sunanta ka daga min kafa amma sabo da ka Raina sirikarka kayi shuru,ai da nace bazan sake magana ba wlh nayi zuciya tunda kaki kulani sai dadinka Kai kake ji,wlh sai na fadawa Mima abinda kayi min tunda baka da mutunci,Arham yace nine bani da mutuncin? Ashe zanzo na Kara yin wani haka kika ce min yaro ne,tun kafin kayi Nisa nace na gane babba ne Kai da girmanka da shekarunki ai sai a karbi tubana tunda kaji haka ai kasan nayi nadama. Kiyi hakuri baza ki gane bane idan ana Jin wannan dadin ba a iya tsayawa ni ban San me nake yi ba,ka haukace kenan? Yace ai sai dai a kira hukumar dawanau lokacin,nifa ban San a Ina nake ba ma,duk dadin dakin Nan ka manta? yace ae ban sani ba a sama nake,a kasa nake,duniyar wata naje,duniyar taurari naje,duniyar rana naje oho Nidai ban sani ba,ko sunana na manta lokacin,in kika ce Arham ko amsawa bazanyi ba Kuma da zaki ce Tijjani sai kiji na amsa Kinga ai sai dawanau na haukace, to me kake ji? Wani azabar masifar dandano ke ni ban San ma me zance ba ni kawai nasan me naji,Allah sarki Dan Uwana Shaheed ana can ana wasi wasi a rai sai dai a Kalli na social media na tausaya Maka,yarinya dole na sake rike ki Kam,Basma tace Dan girman Allah a'a kayi hakuri ka rike ni sakwa sakwa ma ya naji bare Kam,ni ayi hakuri,baya baya wlh daga nesa nesa, tsakanina da Hallare sai mugun fata,har Ina wani karramata na shafeta na...na... bazan Kara ba,Arham yayi dariya kamar me yace ke da zaki Kara sonta kalleta fa,Basma tace wlh zan tsine mata kayi can da ita. Basma kasa tashi tayi har yayi wanka ko motsi,yazo dagata sai kuka a haka ya goge mata jikinta da towel da ruwa me dumi ya gyara wajen,ya zubo ruwa me zafi ya saka towel a ciki wai a haka zai gasa Badon. Daga kwancen ya dinga matse towel da zafi rau ya nana mata,ta kwala ihu..... Naila tunda ta tashi tayi wanka ba abinda tayi a gidan,Spark yaje Office ya dawo tunda yaga ko Oyoyo babu yace sannu madam Yana bin bedroom din da kallo shi da yasan kullum in ya dawo kamar a lashe ko Ina haka yake gani,amma tunda kullum tana yi dan rana daya bata yi ba bai ma dace yayi korafi ba" sai yayi shuru kawai,ya shiga wanka,Yana fitowa da towel Yana goge gashinsa yaji Naila tana kuka,murmushi yayi yasan abokin fada take nema,sai baiyi magana ba,tana kallonsa Yana boye dariya tasan da ita yake,ta Kara Jin haushi tana goge hawayenta, in tana Jin masifa in ba kuka tayi ba bata samun lafiya,kullum sai tayi kuka take sauka,shahada yayi yace me kika dafa? girki aka auro ni nayi me aiki tayi ko sai nice lallai zanyi abinci,yace shi yasa abokinmu wani aurensa ya mutu Ashe matarsa ciki ta samu irin wannan bai sani ba ta dinga shuka rashin mutunci ya saketa sai bayan ya saketa aka gane ciki ne da ita,Naila tace wlh ba Wanda ya isa ya sakeni a gidan nan,wlh ko an sakeni bazan tafi ba na rantse da Allah,Kuma sai na cinnawa gidan nan wuta du mu kone,Spark yace sannu,ka daina min sannu Ina lafiyata kalau Ka dinga ce min sannu Ina Jin haushi fa hakuri nake Ina dannewa,sabo da anga Ina da hakuri na gaji Babana,Spark ya mika mata lotion yace shafa min ni sarkin hakuri,karba tayi ta zauna a bayansa,kafin ta fara sai da ta gwada hakoranta a bayan Spark ya mike ba shiri da cikin Nan ta cije shi yafi a irga,dariya tayi kamar ba ita ba,yasan indai tayi kuka to masifa ta ranar ta kare Kuma,amma in tana so tayi kuka ko waye a gidan a gabansa zata yi kukanta kamar me aljanu. Yi hakuri kawo na shafa maka, ya zauna ta shafa Masa daga shafa mai ta zarce,yace yunwa nake ji tace Nima ita nake ji ayi min haka wlh ko Kuma yau ba Wanda zaiyi bacci a dakin nan,yace Dan Allah kiyi hakuri ni wannan Baby din Allah ya bashi hakuri,bazan Masa baki ba,haba uwar gida? Kana da Amarya kenan? Yace na Isa ai daga ke ba Kari,kece kawai a raina Baby me dauke da Baby ga Kuma Babynta a gefe,kawo min abincin? tace to ta mike taje har abinda ba ayi niyya ba sai da aka kawowa Spark. AsmaBaffa [2/29, 8:59 PM] AsmaBaffa: 🏫TANTIRIYA🏫 A GIDAN YARI BOOK 3 ~~TAIMAKO~ 56-60 Official By AsmaBaffa SADAUKARWA NE GA AIDA MAMAN TASNIM PAGE NAKI NE Hajjora Investment Spark Yana gama ci Naila ta haye cinyarsa dariya yayi,Naila ta shagwabe fuska harda Jan yaji kamar mayya tace Danka ne yake so ba ni ba bare kayi min yanga,Kuma yace ayi sosai deeper and Deeper,shi Babyn? tace ae mana shine ya fada min yace ace please a sa Energy, yace yasan ubansa da Bado ba Sanya,dariya Spark yayi ya furta ai ni sai yanda Allah yayi dani Kuma yanzu,Naila ta fara kissing dinsa kamar zata cinye shi,tana kullum kyau kake karawa kana Kara zagi,tana Saman cinyarsa ya mike da ita ayi standing position Baby yau na nunawa Baby ubansa yayi aiki da Energy,Naila tace no kar aje a zubar min ciki wlh yanzu ba kowanne zanyi ba tsoro nake ji kar Dan ya fice,Spark yace idan an rubuta zaizo duniya ba abinda zai hana,tace nidai ban yarda ba ayi min na me ciki,ai bai tsufa ba cikin,tace tunda kana so ayi kar azo ba ayi bama ya zube, Inshaallah ba abinda zai faru ki yarda da Allah. Mohsin kuwa Allah yayi ya dage zuwa Saudiyya ya so tafiya da Beauty amma ba hali tana da jego,tun daga suna bata koma gida ba tana gidan Abba sai ya dawo zata koma. Washe gari Spark da Naila gidan yari suka tafi Kai Ziyara wajen Mummy,Spark yace idan Kinga zanyi kuka ki lallasheni,dariya tayi tace haba dai Baby kuka Kuma? Yace ae mana. Suna zuwa ana ziyara ga Maza Nan ba a fito da matan ba,Naila ta dinga rokon Spark ya bari su gaisa da mazan da kyar ya yarda,suka fito tare ta Sha Abaya me tsadar gaske,kana nan kaya ne a jikinsa komai fari Kal har takalminsa Snickers,sai kallon su akeyi mazan Nan kamar zasu cinye Naila da Ido,Hannunta Yana cikin nasa,Malam Jilani ta gani a zaune da wani yazo Masa suka karasa,Spark ya mikawa Hannu yace Oga ya gida ya kwana biyu,Naila tace Ina yini? Murmushi Malam yayi yace marar ji Allah ya shirye ki ashe,lafiya muke,dariya tayi sosai Malam Jilani ya lalace wajen kallonta,tace Banga su Malam Garzali ba? Yanzu zaki gansu,kafin ta rufe baki sai gasu sun fito,Spark a dole ya bari kamar zai hadiyi zuciya,kansa ya dauke ya Kalli wani wajen kawai,Naila ta gaisa da su suma,Jakarta ta bude ta fito da kudi ta dinga raba musu,suna ta godiya,duk Wanda tasan suna Shan wahala sai da ta basu kudi da yawan su wasu sun samu duk da baza ka iyawa kowa ba,Goje ne ya karaso yace Allah ya ja zamanin Dahara,murmushi Naila tayi tace ya kwana biyu ya kuke? Goje yace muna Nan lafiya kin barmu ai ke Kam kin ci gaba kin gama damu,ba a taba rainawa gidan yari hankali da ma'aikatan Baki daya ba irin wannan,gashi kinyi aurenki muna miki fatan Alkhairi tunda mu bamu samu ba,amma munyi target iya target ga me sa'a nan ya samu. Spark ya sake yin yamma da kansa ya basar Kuma Yana rike da hannunta,Dan Indo an sake shi amma yaci uban wahala,Yana zuwa ya Kalli Naila ya hadiyi yawu kasa magana yayi sabo da haushi bai samu ba shi,yaki kula Naila,Naila tace Dan Indo ya kwana biyu yace ba dadi kawai Yana magana kamar zaiyi duka,Na gaishe ka sannan na gode Maka da taimakon da kayi min,yace na janye abina dama rashin Sani ne ya sa karki sake gode min da nasan ke macece wlh bazan yi ba,badan Allah nayi ba yawwa kar a sake gode min ni,Naila tace ai kuwa ni bazan daina gode Maka ba,yace bakinki ne yake aiki anyway naji dadin ganinki haka Allah ya taimaka,Kai Kuma Ina bakin ciki da samunta da kayi domin bana Maka murna ka cuci mutane kawai,kazo ka damu mutane a gidan yari Allah ya tsinewa Wanda yayi silar shugowarka gidan yari,da yanzu baza ku hadu da Jamilu ba,kazo ka wani dinga gyarawa mutane gidan yari harda yiwa mutane tuka tuka iri iri bazan Sha ruwan ciki ba bare ka samu Lada na" ta gomnati zanje na Sha,tuni ma na balla kofar da da kanja a dakinmu ba a so,Spark dariya ce ta kamashi ya juyo ya Kalli Dan Indo yasan tsagera ne basu da kunya hukuma ma sun gagare su,yace kanka kayiwa ya jawo Naila Jikinsa harda rungumeta tare da gyara mata mayafinta,tsaki Dan Indo ya ja yace yanzu haka ma ciki ne da ita ko? Spark yace fada Masa Baby,Naila tace na Dade ma ban samu ba da ace na samu da wuri da tuni fa na juye amma yanzu Alhmdllh wata hudu. Dan Indo ya hade rai ya bar wajen,Washer da Scola ne suka karaso wajen suna karairaya,Scola Yana Yar uwa.......Naila tayi dariya tace Scola ga washer Allah ya shirye ku,Scola yace Ameen Dan manzon Allah,Oh Jamilu duniya sabuwa haka aka koma kamar wata Gold,muna Nan muna kewa,Washer yace ke Yar uwa amma ciki ne da ke? Mu dai Kinga duk Daya muke fada mana madarar Nido ta cika alkawarinta taje Inda ake so? Naila tace yanzu ma nayi amai,Scola yace a wallahi sagwo dake,Dan Allah ki haifo Yan biyu,sannan a fada mana muna daga nan zamu yi suna,Naila tana dariya Hira ta carke tsakaninsu sai zuwa suke ana gaisawa Wanda ya dace a bashi tallafi. Scola yace to ni baza a bani kudin ba? Naila tace kana da karfi Kai,yace wlh sai kin bani naci kudin wannan Dan duniyar ya daki Kafadar Spark,yace wannan Dan iskan idan yazo shi kadai ko hira ba a yi da shi wai shi babban yaro, Spark yayi murmushi sabo da ya Saba in yazo indai sun hadu da mazan sai wasu sun zazzage shi da wasa. Scola ya karbi kudinsa yace iceko kina Shan kiss Tantiriya? Naila tace sosai sau ashirin,ah ai ko sabon aure ta samu kiss sau ashirin a rana ta godewa Allah,Nima Ina so na tuba inshaallah daga Daudu sha'awa kuke bani in Allah yayi zan tuba,Allah ya sa cewar Naila. Yau Naila taji dadi ta gaisa da mutanenta sai murna take yi,Maza suna komawa aka fito da mata,Mummy ce tazo tare da Yar Uwarta Maman Wahida,Spark ya Kalli Mummy duk da dai ta canja amma bai nuna tana Shan wahala ba,amma sabo da shagwaba ganin Spark har da fashewa da kuka,Spark suna zaune Mummy ta zauna tana goge hawayenta,Spark yace kiyi hakuri Mummy,wannan dalilin yasa naki zuwa da tun farko,idan Kuma ba Kya so na dinga zuwa to shike nan zanci gaba da miki aiken,na daina tace sannan suka gaisa ya gaida Maman Wahida ta zazzage shi tace wato ni ba uwarka ba ce? wai ace ka kasa zuwa wajena har gidan nan kake zuwa,duk da nasan nayi kuskure nice nayi sanadin shigarka gidan yari ka yafe min Dan Allah. Spark yace na yafe miki tuntuni ni kawai idan na tuna to be honest Ina Jin haushinki amma komai ya wuce Inshaallah bazai sake faruwa ba hakan,take away din suka basu sannan sai ga Mima da Maman Rafeeq suma sun kawo ziyara dama su suna zuwa,har Baban Misam Yana zuwa sosai,Maman Wahida tace ga yata nan bikinta ya kusa Spark, Wahida ta samu mijin aure zata auri wani lecturer Kuma matashi ne wlh kyakyawa da shi ga kyan Hali,bikinta watan gobe,yace naji Mima ta fada min Allah ya kaimu lokacin tace Ameen. Sun dade suna hira kafin su tattara su tafi,Spark shi kauyen su Naila suka wuce wajen su Goggo. Mima da Maman Rafeeq kuwa sai suka wuce gidan su Naila basu taba zuwa ba za'a gaisa,suna zuwa Napep suka shiga suna kiran Kubra a waya da haka suka je gidan,Abba suka wuce a Saman katifarsa Yana shago,sun zaci Bai da lafiya dan fitowa yayi shakatawa,Mima tace ga Baban Nailan ma suka leka shagon,Abba yaji kamshi na daban,ya toshe hancinsa yace Haram naji kamshi Kuma Muryar mata,ku dinga Jin tsoron Allah in zaku fita ku daina saka turaren,ku kiyayi hancin Maza ya jiye muku kamshin jiki,wlh babu kyau,duk yanda za ayi wani turaren ajiyar kaya,turaren jiki,da sauransu in ya kama Mazaje suka shaka haramun ne Allah zai muku hukunci,yanzu an dauki wannan wayewa sabo da kawai kina da kudi ko kina matar wani me kudi sai a dinga shiga yanda aka ga dama ana baza kamshi a gari sabo da me kudi shi Gani yake baya yiwa Allah laifi,duk gashi a waje ana gani ko a saka Yar Abaya da guntun mayafi shape duk ya fita maimakon a saka mayafi babba a cire na Abayar baza ayi ba,shi yasa Yar Inna take birgeni wlh ko Abaya ta siya sai ta siya mata mayafin daban Kato Kuma ba kyau aka fita ba,wani fito da sura da kamshi ba shine yake nuna ke yar gayu bace,akwai wankan da mace zata yi cikin sutura Kuma ta fito a Yar gayu ta gaske ba tare da surarta ta bayyana ba irin Yar Inna,duk wannan surutun da Abba yake Bai ma Kalli matan yasan su waye ba,sai da Mima tace Babar Spark ce, Abba ya juyo yace to sabo da Babar Spark ce baza a Fadi gaskiya ba,Maman Rafeeq ta share zancen tace baka da lafiya ne muka ganka a katifa a shago? Abba yace haka nake sana'a ta wlh Inlaw,yanzu in ka sake sai Basir ya Kamaka akan neman kudi,Nan Yar Inna in taga dama tana zuwa ta tayani hira idan Yan mutuncin suna kanta,Mima tayi dariya tace to bari mu shiga ciki,yace ai kunsha rana Inlaws ku shiga tana Nan jullof ta dafa,suka wuce suna dariya,Mima tace gaskiya Spark Yana da siriki a nan, kan bala'i a haka wai nasiha yake mana Murya Kuma a sanyaye,dariya suka sake yi Maman Rafeeq tace bawan Allah bai iya fada ba daga ji wlh irinsu akwai dadin zama,ni da zai aure ni ma ya birge ni,Mima ta bude Baki tace ke ki rufa mana asiri kinji daga zuwan mu ya ambaci Yar Inna-Yar Inna yafi sau nawa. Shiga suka yi ciki Zarah tana dauke da kanwarta suna ball da Aslam,ganin Baki suka amsa sallama tare da gaishe su,Kubra ta fito tana musu sannu da zuwa,suka shiga ciki Mima a ranta tace Ashe dai suna da rufin asiri ga gidansu me kyau babu makusa,ko Ina Kal Kal Yana kamshi,gaisawa suka yi suka fara hirar gidan yari da su Mima,sannan ta kawo musu Abinci ga nama soyayye a plate da yawa sai ruwa da lemo,Mima tace bari muyi Sallah tukun,suka shiga toilet tare da yin Alwala suka fito sai Sallah,bayan sun idar suka ci abincinsu suna hira,Kubra tace bari a kira me gidan,mun ganshi mun gaisa ai mun Sha nasiha sosai,Kubra tayi dariya tace sai hakuri fa,suka ce ba komai wlh gaskiya ya fada ai,sai yamma likis suka ce zasu tafi,Abba ya kawo musu nono kindirmo da yawan gaske lafiyayye yace ban San me za a Baku ba wlh duk abubuwan Kuna da shi da ma a kauye ne, Yar Inna a basu su kuka da su kubewar Miya,Mima tace ai kuwa ta Abuja ba a samun me kyau,Abba yace daga kauye ake kawo mana Ita kwano kwano ko ba nama kika yi miyarta su Shaheed sai sun dinga tambayarki Mima Ina nawa Naman sabo da dadinta,ai sunanta Ina nawa Naman,Mima suna ta dariya suka ce a bamu to mun gode,Abba yace ki daka daddawarki sosai ki sa mata Dan tattasai Banda tumatir,miyar kubewa bata son tumatir, suna ta dariya su dai a ransu, Kubra ta kawo musu ita da yawan gaske,ga kubewa busashiya,ga daddawa me yawa,da abubuwa dai na Miya,suka yi godiya,suka raka su sai da suka shiga taxi A haka a gurguje suka nemi gidan Iyalan Yahuza donation suka je suka gaisa Mima har kudi ta basu duk da suna sana'a basa cikin wahala,gwara ma yanzu akan sanda yake raye,yanzu suna samun na kansu suna ci suna koshi sunyi kiba sunyi kyau da yaransu,Ikhy tana taimaka musu. Mima tace muje Kinga tunda mun kusa zuwa kaduna sai muje gidan su Suhailat Chika itama a gaisa. Ana shirye shiryen bikin su Nabeela da Rahma Haidar Mamansa ta dawo,shi ya dakkota a airport tare da Mijinta,Hotel da suka kama masaukinsu Haidar yace shi gwara a kama musu gidan haya tunda zasu dade a gari,amma Mamansa tace me gidanta Dan hutu ne ya Saba da rayuwar turai haka ya kyale su,kwanansu uku a gari kullum sai taje gidan Jauro sun gaisa,Haidar suka tafi Abuja shi da Mamansa su biyu,gidan Rafeeq suka sauka,Rafeeq sirika tazo da wuri ya dawo daga Office suna kama da Ikhy dinsa da Maman Haidar,ga Ikhy ciki ya girma sosai da sosai ana ta ja,Haidar Yana parlon Rafeeq suna hira,Rafeeq yace Mufee kuwa tana yawan tambayarka,Haidar yace uhm Kanwarka yanga take min,kazo muje kawai na kaika daga yau baza a sake Maka yanga ba,kasan mata haka suke Yar banza ce ai,Haidar harda kamewa ana kunyar Rafeeq ya zaci wani na kirki ne,sai da Rafeeq yace tashi muje Yar banza aure take so na sani yanzu da zaka taba ta gani zaka yi tana lumshe Ido,ai na kiyayi Yan gidanmu,Haidar yayi dariya yace a'a me zai kaini tace min Dan Iska sai anyi aure,Rafeeq yace tab kana da aiki amma bari ku saba sanda za a dinga dandane Ina gidana ni,kawai dai ana so a daure sai anyi aure sabo da mata akwai zargi baka taba su ba ma ya aka kare bare ka taba su tana jinka da wata ko ka tafi wani wajen zarginka zata dinga yi abinda kayi mata fa shi kake wa wata ma,to sabo da kaucewa irin wannan gwara a kiyaye tabe tabe Nan kafin aure duk da ni nayi amma nasan shedan ne,Haidar Yana dariya yace ai zuciya da shedan akwai ingiza me kantu ruwa Allah yasa nafi karfinsu,ko zan fi karfinsu ko bazan fi ba oho,Rafeeq yace baza kafi ba da alama Kai ba a iyawa, naso nayi karo da shedan na kasa ya bugar Dani,to yanzu dai ga matata Allah yasa itace kawai Kuma na auri Abata. Haidar a dakin da aka bashi yayi wanka ya canja sabon kaya dal shadda milk ya Sha kyau Yana kamshi,har takalmi ya canja suka fita a motar Rafeeq,suna zuwa ba Wanda ya sani Rafeeq ya kaishi palon baki ya shiga wajen Mima. Mima tace lafiya na ganka yanzu me Ikhy,Yace wajen Mufee nazo Ina yini? Bayan sun gaisa tace tana dakinta,dakin ya shiga ya samu Mufee tana tunani haka kawai,yace ke Kuma me kike tunani? Yaya mu Munki samun miji wlh aure nake so Nima,Allah zanyi ta Arham Nima a aurar Dani,Kizo to ai ga mijin yazo Malama,Haidar dinki yazo Yana jira,wato yanga kike Masa a zamanin nan,Mufee tace shugo kaji Yaya,shiga yayi ya zauna tace Yaya Ina sonsa wlh baida Matsala amma kawai samunsa da aka yi Bata aure ba shine matsalar,ke da aka same ki ta hanyar auren finsa tarbiyya kika yi? Irin wannan ko a wajen Allah Basu da laifi,suma tashi suka yi suka tsinci kansu a haka,yanzu kika San irin bacin ran da yake ciki? idan ba a jansu a jiki ana kyamar su ana korar su ta ya zasu nutsu su zama na kirki,ba fa laifin su bane,ki auna abin a kanki idan da kece haka ta kasance a kanki ya zaki yi?kin waye kina da Ilimi bai kamata ma kice haka ba,ke da kinfi su Haly ma hankali gaki kyakyawa kinfi matan gidan kyau mune kadai baza a fada mana kyau ba domin Ikhy dita tayi dace,Ikhy Rafeeq ta dace,dariya Mufee tayi tace yanzu ta koma Ikhy Rafeeq Kuma? Yace ae ta koma haka,ki tashi kije Yana jiranki gaki da abin gari,Dariya tayi ta rufe Ido yace,ato yaran Mima badai baiwa ba mu gamu da Hallare matan gasu da Uhum hum banda Anam ita Dangin Papa ta yo shegiya kirji kamar plate duk ta damu mutane. Ya kamata dai ki fara koyon zaman aure da girki da abubuwa Dan ku matan gidan gidan nan kwalliya kuka iya,Mufee tace ai na fara online Kuma Ina gwadawa haka Haly ma,yace yafi muku idan kunki Kuma mu kira Basma ta koya muku,Mamanka tana gidan tun safe Arham zai kashe Yar mutane yanzu ba a San a halin da suke ba ance dai wai asibiti za a kaita,Rafeeq yace Iyyeee ni naso nayiwa Ikhy haka amma yarinyar nan ta shanye zafin Bata samu matsala ba kaji yaro Arham da nuna Jarumta Kai amma ya birge ni wlh, Dole na labartawa Misam da Spark wannan bajinta ta kaninsu,Rafeeq sai dadi yake ji kamar shi yayi abin. Mufee kwalliya ta chaska ta wuce wajen Haidar. Arham kuwa Yana saka towel yaji Basma ta kwala ihu yace ai kuwa dole ayi miki,yaci gaba Yana cewa sorry Sunshine,a hankali zan miki,ya sake matsewa ya manna mata ta zabura ta rike shi tana rokonsa please,sai da ya Dade Yana gashi sannan ya dai ya Maida komai toilet din ya wanke ya fito,ta danji dama dama amma har yau dai baza ta iya tashi ba,haka suka kwana da kyar suka yi bacci,da safe ma kuka ta dinga yi Masa,ya rasa Inda zaiyi da ita,taki yarda ya dauke ta,Mima ya kira,Mima tunda taga kiransa da sanyin Safiya tasan da matsala,dagawa tayi yace Mima kin tashi lafiya? tace lfy Alhmdllh...kafin ta sake magana yace Mima kizo Dan Allah Basma ce ta kasa tashi daga dan yin abu,Mima tace ai nasan haka zata faru Kai baka da hankali kasan yarinya ce fa,Nima yaron ne ai Kuma na Sha wahalar nima,Mima tace naji ga Maman Rafeeq Nan zata zo,a'a karta zo wannan da ta samu a gaba tazo ta sake yi mata mugunta,to ka zauna da abarka haka,sorry Mima tazo to,Kashe wayar Mima tayi ta sanar da Maman Rafeeq,driver ya kaita gidan. Tana zuwa Arham ya bude kofar yace Ina Kwana Mama ta Harare shi tace Ina Basma din? Yana murmushi yace tana ciki tsohon hannu,kune tsofaffin hannu,wucewa tayi ciki ta kyale shi,Basma ta samu tana kuka,tace Allah ya Kara ke ba marar kunya ba kin biyewa namiji,Mama ta dagata Basma ta dinga kwala ihu,Arham ya shugo yace ayi mata a hankali taci wahala jiya,Mama tace wlh idan ka dameni da fitsara zan tafi,sorry yace, ta kaita toilet tana cewa ki karfafa jikinki raguwar banza,Arham ya leka yace ba raguwa bace wlh ai jiya tayi Jarumta,Kofar Mama ta rufe ta sa key,sai da ta tayi mata gashi sosai tana faman kuka,Mama tace dole a kaiki asibiti wlh da alama sai likitoci sai sunyi agaji,a gurguje ta Dan shiryata sama sama zama ya gagara bare tayi Sallah da kyar tasa tayi Sallar suka tafi asibiti. Suna zuwa Likitar tasu ta duba ta tace wai wannan yayi aiki wlh,ta duba sosai tace ni nafi tunanin ayi mata dinki kawai zai fi,idan an barta a haka zata warke normal amma ayi dinkin yafi Alkhairi,Mama ta fadawa Arham yace a dinke min ita in da hali a dawo min da ita virgin sabo da jiya na Sha ragadada,Likita tace Allah ya shiryi wannan yaro nidai naga ta kaina,Mama tace Ameen ayi mata dinkin. Ai kuwa aka tafka dinki,Basma taji azaba iya azaba,Mima bata fadawa kowa ba babu Wanda yasan me ake ciki,su Haly ne kawai suka San halin da ake ciki sabo da sunji Mima tana waya tace wlh in suka fada tam dinsu. Amma Dake ba a sirri da su Shaheed Yana zuwa suka fada Masa a boye suka ce kar ya nuna ya sani,Shaheed ya kira Arham yace shege mutumina Allah Sanya Alkhairi irin wannan aiki haka,Arham yayi dariya yace ai namiji ne ni....an barka a baya Shaheed ka dage da rashin kunya ayi Maka aure wlh kaji na fada maka ka samu wata ko Yar dukurkurar ce a daura ma,Shaheed yace ni bana ra'ayin auren wuri sai na Kai kamar Spark ko Misam,yanzu a tara min yara haka kawai su isheni da Baba...Baba...siyo min Madara..Baba siyo min alawa....Arham yace tab da yarana zan girma in na tsufa Ina da masu kula dani Allah ya bani na gari masu Albarka ayi ta haifo min,ka sani ma ko juya ne Kai kake iyayin wani zaka haifi yara,watakil ma Maman Rafeeq ka gado sai dai ayi ta asarar Nido,Maman Rafeeq ta harari Arham tace wlh badan Mima ba bazan zo ba tunda baka da mutunci Kai fitsararre ne,sai dare suka baro asibiti suka dawo gida da dokokin Likita. Take away Arham ya musu Mama tace Ina Nan za a kawo min kayana wlh tare zamu kwana da ita sai ta warke Dan ubanka,Arham yace wai nifa ba ke kika raineni ba kije gidan Rafeeq mana sai ni,Kayi ka gama zama daram ta mike ta shiga kitchen,tana shiga kitchen Arham ya zauna ya Maida Basma jikinsa Yana lallashinta,tace ba Kaine ba ai duk laifinka ne,ka kira min Umma ta ni,yace Amma ba fada mata zaki yi ba? tace ae bazan fada ba ai,bayan ya kira mata Ummanta sun gaisa sai ga Mima tazo da abinci da kayan ciye ciye. Mima tace sannu Arham yace yawwa Mima ,harararsa tayi tace Kai baka komai a nutse baka tafiyar da lammura dai dai? Wato baka da hankali ko zaka illata Yar mutane,Arham yace sabo da Allah a kasar Nan mene ke tafiya dai dai yanzu in banda agogo,agogo ne kawai yake tafiya daidai ko na waya ko na bango duk daidai suke tafiya, da ka saita abinka baya gocewa,Mima dariya tayi kawai sabo da masifar zaro zancen Arham,shi da Spark ba a kada su a magana. Haneef da kansa ya Maida Mero gida ya gaida Iyayen Mero,Jummai duk ta haukace Taga me kudi ta zauce,ta ebo awara cikin plate da yaji a gefe ta kawo Masa me zafi,ta sa aka siyo Masa ruwa da lemo,Haneef haka yaci awara Yana tunanin undee din da aka tace da shi,ba yanda zaiyi ya fuske yaci uku,ya Sha ruwa da lemo,Baban Mero yazo shima suka gaisa,Haneef ya musu Sha tara ta arziki ya tafi tare da bawa Mero kudin kashewa yace ta tambayi ranar da zai turo kudin aure. Jummai tafi kowa murna sanda Mero ta fada musu shi zata aura,Nan take Jummai tace ya turo sati me zuwa ba ruwanta da Baban Mero,Mero tace baba kai wacce rana ka zaba? Yace duk abinda Mahaifiyarku tace yayi,Mero tace hmm kawai. Kafin sati a kawo kudi Mahaifin Mero ya fara cuta sama sama suna kaishi chemist amma Abu ba sauki,Jummai hankalinta ya tashi tana son mijinta ashe iskanci ne,sai ta zauna tayi ta kuka,Mero tace mu tafi asibitin birni,washe gari da safe suka tafi asibitin Nasarwa,kudin test kansa sai da suka siyar da gonar Sani sannan aka samu aka yi Masa wasu test,Mero kullum suna waya da Haneef Bata taba fada Masa ba sai dai tace lafiya suke. Ana gobe zai turo Mero ta kirashi tace babanta baida lafiya a bari sai yaji sauki,yace ba damuwa ta hadashi da Jummai ya mata Allah ya sawake,duk ya zaci ciwon karami ne,shi Kuma Haneef Mamansa tace bai Isa ya auri Khadija ba sai dai ya canja wata,fushi yayi ya kashe wayoyinsa gaba daya Dan kar ma ta neme shi ko zai samu ta sakko,Yayin da Mero sakamako ya fito cewar aiki za a yiwa Babansu amma sai ya lashe 3millions,Basu da Sisi,na asibitin ma da kyar suka samu,Jummai kuka take kawai tace yanzu Ina zamu samu kudin gashi Likita yace idan ba ayi ba mutuwa zaiyi,Mero tace gashi wayoyin Haneef basu shiga na rasa dalili,bari naje gidansa tunda a Nan Kano muke,Munnir kanin Mero yace Yaya Khadija ki guji zuwa gidan namijin da bashi da aure wlh,komai zai iya faruwa dake,ki daina biyewa Inna,namiji baida mata gidansa shi kadai zaici me kyau ya koshi ga kudi" me zai nema in ba mace ba,ita zuciya bata da Kashi da kike Ganinta bare Yana sonki kina sonsa komai zai iya faruwa. Nidai wlh bana so naji kina zuwa gidan namijin da bashi da aure komai tsoron Allah dinsa,har kullum shedan Yana nan,Jummai tace rufe mana baki ko na mangareka,idan Bata je ba da ubanka za ayi masa aikin,zaka yi mana mugun fata. Mero tace bari dai naje nasan zai bani,ta fice sanye da hijab dinta har kasa ta Isa gidan Haneef, Kwanan Haneef uku baya Jin dadi baida lafiya Yana kwance a bedroom Khadija ta shiga,Iro Yana mata sannu da zuwa,tace Salamatu tana gida? Yace bata nan ta tafi kauye ganin danginta sai dai Oga yana ciki kwana uku baida lafiya,Mero hankalinta ya tashi ta nufi ciki da sauri,direct bedroom dinsa ta nufa ta hango shi akwance yayi shuru kawai,sallama tayi ya kalleta a hankali tare da lallabawa ya mike zaune yace yaushe kika zo? yanzu nazo" aka ce baka da lafiya? Naji sauki ai ya furta yace lafiya dai naga kin dan rame kamar kina damuwa? Mero tace ka kashe wayarka ba a samu Babana ne baida lafiya har yanzu aiki ma za ayi Masa Kuma gashi million uku sunce idan ba ayi gaggawar yi ba Nan da kwana biyu zai iya rasa ransa,Mero ta fashe da kuka tace Dan Allah ka taimaka mana ayi Masa ya warke Dan Allah,Arham yace mene na roko na haka ya jawo check ya rubuta mata million uku da rabi yace gashi,bana Jin dadi yanzu shi yasa bazan iya zuwa na biya komai ba kiyi hakuri kije ki biya,Mero sabo da Murna ta fada Saman bed din ta rungume Haneef,tana godiya bata San matsalar Haneef ba mace yake nema wanted itace cutar duk maganin ma yaki Masa aiki,Yana samu ta tabashi shike Nan ya zauce ya fita a hayyacinsa ya fara kissing din Mero Yana shafe mata jiki,Mero tun tana kwatar kanta suna komawa tana rokonsa ya bari sai anyi aure Ina ba ya ji,ya fita karfi,kasa komai tayi ga son juna da feeling din juna Yana Kara assassa abin,yana lallaba Mero Yana rokonta Yana kalallame ta,Mero kuka take kawai tana jinsa gashi itama abubuwan da yake mata baza ta iya hanawa ba ya samu dai ya raba Mero da kayan jikinta,Shima ya cire nasa,yana sarrafa Mero yanda yaga dama a rude yake ya shigi Mero sosai,Yana gurnani Yana Sambatu da Nishi,Mero sai wahala da ta Sha tana ture shi tana kuka amma sai da ya Kai gaci Yana zuwa zai kawo ya haukace Allah ya bawa Mero sa'a ta kwace jikinta ya jawota ya mannata a jikinsa a haka yayi barin madararsa a waje Jikin Mero,Allah yasa baiyi a ciki ba ta kwace kanta. Sai Nishi yake Yana Jan numfashi da kyar tare da sake kankame Mero a jikinsa. Khadija Kuka take Wiwi kamar ranta zai fita,tace dama sabo da nazo neman taimako wajenka shine ka keta min haddi,da me yasa baka neme ni ba sai da na zo neman Taimako,bana sonka na tsaneka wlh bana sonka ta mike da kyar tana tafiya da kyar ta Maida kayanta jikinta tana kuka,Haneef kansa ya Kifa ya fashe da kuka sosai marar misali,yace ki saurareni Khadija ba haka bane,ki tsaya kiji,Khadija ta duka ta dauki check din da ya rubuta mata Kuma tace bana sonka na tsaneka,nayi dana sanin saninka a duniya,Kai ba Alkhairi bane,na tsaneka fasiki,daga zuwa neman Taimako" ta juya da takadar kudin Kuma ta tafi tana hawaye tana tafiya da kyar,check Yana hannun ta,Arham kuwa wani mugun lafiya yaji ya samu amma ya rasa abinda ke Masa dadi a duniya. Iro me gadi yaga Mero ta fito tana takawa da kyar Kuma tana kuka yace lafiya Mai nauyi? Mai nauyi me ya faru? Mero ta fice abinta tana tafiya a kafa da sauri ta shiga napep sabo da burinta ayiwa Mahaifinta aiki,tana zuwa asibitin ta samu Innar su,Munnir,da wasu dangin mahaifinsu suna ta kuka ana Allah yaji kansa,Sani ya riga mu gidan gaskiya,Jummai ta rugo da gudu wajen Mero tana cewa ya rasu wayyo na shiga uku na lalace Khadija,Baku da Uba yanzu,ubanku ya rasu..... Khadija Mutuwar tsaye tayi kawai hawaye na zuba a idanunta ta ja kafarta a hankali zata juya ta zube kasa a sume. Salati aka saki tare da daukanta aka dorata a gadon asibiti aka Bata agaji har ta farfado,lokacin an Bada gawa ma dangi sun tafi gida da shi,Jummai ta bisu daga Mero sai Yar uwar Jummai tana jinyar Mero,tana farfadowa,matar tace idan zaki iya ki tashi mu tafi gida,aka sallami Mero tana kuka suka fito,Mero bayan sun shiga Napep ta gwada Masa gidan Haneef ya kaisu tace ku jirani na fito,matar tace to suna tsaye da me napep suna jiran Khadija,Shiga tayi ranta a bace,fuska ba annuri,a Palo ta samu Haneef a zaune ya Sha wanka fes da shi ya warke amma ya hada Kai da gwiwa yayi tagumi,sallama tayi ya dago a firgice tare da amsawa Yana karewa fuskarta kallo,idonta ya kumbura,fuska ba annuri,kafin yayi magana ta mika Masa check dinsa tace karbi,ya manta ma ya Bata check ya karba tace ga kudinka Nan Allah ya Masa rasuwa tana fadar haka ta juya ta fice Yana kwala mata kira ko Juyowa Bata yi ba tayi tafiyarta ta shiga napep suka tafi gida. Haneef tashi yayi ya kira driver ya dauke shi suka nufi kauyen su Khadija Shima. AsmaBaffa [3/2, 8:30 PM] AsmaBaffa: 🏫TANTIRIYA🏫 A GIDAN YARI BOOK 3 ~TAIMAKO~ 61-65 Official By AsmaBaffa SADAUKARWA NE GA AIDA MAMAN TASNIM PAGE NAKI NE Hajjafatty Haneef ya riga su Mero Isa kauyen ma,suna zuwa suka ga motarsa acan har an yiwa gawa sutura za a tafi kaita da shi aka tafi kaita,Khadija tana ta sharbar kuka biyu ga na mutuwa ga na abinda ya faru da ita,gidansu a cike da Yan uwa da abokan arziki,Khadija ta shiga ciki ana ta bata hakuri ana mata ta'aziyya ko amsawa bata yi gado ta samu ta kwanta tana ta kuka. Jummai kuwa sai sambatu take yi Allah yasa mun rabu da Sani lafiya,tunda muke dama shi Sani baya fada baya fada dani sam ,ko Abu yaga nayi ba daidai ba sai dai ya nema min shiriya wajen Allah,masifa ta same mu rana tsaka,mutuwa me Yankan kauna,ta rasa Ina zata je sai gidanmu ta rushe da kuka,ana bata hakuri mutane suna cewa sai hakuri,haka Allah yaso,Maza suka dawo daga janaza ai kuwa sai ga Haneef ya shugo har ciki yayi gaisuwa,yace Ina Khadija? Akace zazzabi take baza ta iya fitowa ba,yace to ayi mata ta'aziyya duk da haka sai da Jummai tace shine Wanda Khadija zata aura ai take fadawa mutane,badan ya so ba haka ya juya ya fita kasa tafiya yayi ya zauna wajen makoki abinsa. Sai wurin dare ya tafi ransa a bace zuciyarsa kamar ta fashe sabo da bacin rai da bakin cikin abinda ya aikata. Khadija haka zuwa dare ta lallaba tayi wanka tare da tsarkake jikinta tana kuka tayi sallolinta tana ta addua tare da neman yafiyar Allah, shine ma ta samu sassauci ranar a haka ta kwana,washe gari Haneef duk yanda zai ga Khadija abin yaki ta boye kanta a daki,har aka yi Sadakar Uku bai ganta ba kullum sai yaje Kuma,su kuwa Yan gari Jummai kawai ake zagi ana yi mata Allah ya Kara,suna cewa yanzu maga Inda zata sa kanta,zamu ga ya zata yi,abinci ma sai ya gagare ta,Wanda basu San shi Allah ba haka yake ba. Bai sake zuwa ba sai da aka yi Sadakar Bakwai,Yana shugowa gidan ya ga Khadija,wani Sanyi yaji a ransa,tana gyara wake duk ta rame,tana Jin muryarsa ta fashe da kuka ta mike ta fada daki tana rusa kuka,Jummai tace lafiya Yar Nan kamar Kinga maye zai lashe miki kurwa,wannan kuka naki Mero na rasa dalilinsa,ko ni da nake Matar ubanki nayi hakuri nayi tawakali amma ke kinki bafa zai dawo ba,Munnir ma ya hakura,Haneef ya durkusa a kasa,Jummai tace tashi Dan Allah ga tabarma yaron kirki,ta karkade Masa tabarma ya zauna. Da ladabi ya gaishe ta tare da Kara yi mata ta'aziyya,tace an gode fa da hidima ga kayan abinci suna tafe ga kudi Allah ya Kara budi,yace ba komai,Jummai tace shiga dakin nata tana ciki zafin mutuwa ne watakil taji maganarka kai. Haneef tashi yayi ya shiga dakin Mero ba komai a ciki sai ledar tsakar daki me kyau sai Yar katifarta karama sai kayanta a Ghana must go a gefe,tsaf tsaf an goge. Haneef ya sameta a kwance tana ganinsa tace ka tafi wlh bana kaunar ganinka na tsaneka,mazinaci fasiki,Idonsa ya runtse sabo da zafin Kalmar da yake ji tana fada Masa,na tsaneka wlh bana sonka bazan aure ka ba macuci,Jummai tana Jin komai amma Bata San dalilin da yasa Khadija take cin mutuncin Wanda zata aura haka ba. Haneef yace Dan Allah ki daina daga Murya,wlh banyi Dan na cutar da ke ba,bani da lafiya ne lokacin da kika zo Ina kan gwiwa,duk zaman da muke yi Ina tare da matsananciyar sha'awa wacce har ta Kai ga ta zuba min lalura a jikina magani ma Likita ya bani amma na Sha banji sauki ba,Ina Baki check kika rungumeni daga lokacin na kasa control bazan iya control ba a lokacin,kiyi hakuri ki yafe min,banyi da niyyar hakan ba,karki manta na San mace tunda nayi aure na taba sex ba sau Daya ba,kamata bazan iya hakurin zama haka ba mace ba,kin San irin macen dana aura,nayi nayi Mama ta bari a daura mana aure cikin gaggawa amma taki yarda shine har Hakan ta faru,Kuma nayi niyyar ana kawo kudin a daura amma mahaifinki ya fara rashin lafiya,kaddara ce Allah ya gani bada hayyacina nayi ba Kuma bada so na ba,Khadija tana kuka tace ai dama komai sai ace kaddara ce bazan yafe ba Kuma bana sonka ka fita ka bani waje,kallonta yayi tace ka fita nace bana kaunar ganinka,kiyi hakuri ...ka fita bana son Jin komai,Haneef ya fita kawai ba yanda zaiyi da ita,Jummai tana kallo ya fice kamar zaiyi kuka,dakin Mero ta shiga ta sameta tace ke kuwa Meke faruwa haka da ke Khadija? Mero tana kuka ta kwashe labarin kawai ya fadawa Innarsu,Jummai kirji ta dafe tace Yau na shiga uku ni Jummai Dan iskan yaro hanci kamar sillen kara,ta tabbata Munnir kambun baka ne da shi abinda ya fada ya faru,Wayyo Ina zan saka kaina ga Mutuwar miji gashi an lalata min yarinya, Jummai tace da me zan ji a rayuwa ni kuwa Jummai,kawai a haka rami a binne ni na huta,Mero tana kuka tace ai duk laifinki ne da son kudi da kin barni a gida ko zamu hadu da shi sai dai yazo gidan iyayena ya same ni gashi yanzu ta karfi ya lalatani waye zai aure ni a haka? Jummai tace shine Haneef din,tunda haka ta faru ai kuwa shi zai aure ki wlh dole,Mero tace bana sonsa bazan aure shi ba,gwara kawai na kama siyar da abincin siyarwa in nemi na kaina,Jummai tace wlh Baki isa ba Khadija ko mutuwa zakiyi sai kin aure shi,Allah ya kawo mana hutu da gata kice baza ki aure shi ba,to ribar me kika ci? Ya lalata ki sannan arzikin baza mu ci ba? Yanzu Ina check din da ya Baki na million uku da Rabin? Na mayarsa Masa da abinsa,Jummai hannu ta daura a Kai tace kin cuce mu,to me kika yi kenan? An lalataki yaci banza,gashi auren ma kince baza ki aure shi ba to ki gaya min ribar da kika samu,Mero tace ai mutunci yafi kudi,Mutunci ya kare tuni Mero tunda ya samu Jikin ki ai aikin gama ya gama tuni yayi wasa ya cinye kwallo,Manchester da Arsenal ai sai buga wasa,Sabo da haka wlh sai na karbi million uku da rabi Kuma aure sai kin aure shi,Mero tace ni Kuma wlh bazan zauna ba,gwara ma ki kyale ni ko na tonawa kaina asiri a gari nace yarki an lalata ta,Jummai ta bude Baki taji tsoro tace Inshaallah ma zaki sakko ki hakura ku rufawa juna asiri,yanzu kiyi shuru da bakinki ko Munnir kar yaji zancen nan Dan Allah bare ya fita gari aji. Dole na gyaraki sosai ya gama dake. Haneef kuwa ya rasa Inda zai saka kansa,ko wayarta ya kira sai dai ta kashe,idan ya tura mata text shuru,Hakan ya Kara tashin hankalinsa ya rasa Inda zai saka kansa. Jummai kuwa yarta take gyarawa sosai ta dole take wa Mero duren magani,kudin da suka samu na sadaka da su Mero ta fara siyar da wake da shinkafa da Miya harda salat a kauyen kusa da Inda mutane suke taruwa,harda kafa katon table da bench dinta na zama,abincin ta zubo a manyan coolers Almajirai su kawo mata wajen tazo ta siyar da abinta,bata shiga safgar kowa ranta a bace yake. Washe gari da sassafe Mero ta rage tunani tana kwance ta koma bacci wani Zakaran gidan su ya hanata bacci da cara,a cikin bacin rai take da takaici,fitowa tayi ta cafke Zakaran tare da zaro Masa Ido ta nuna shi da hannu tare da yi Masa dakuwa zagi ambola tace uwarka nace,shege Dan iska ka dameni,wlh duk ranar da Ina bacci ka dameni da cara sai naci ubanka,ko Dan kaga kwai aka yi aka sameka zaka yiwa mutane wulakanci ta make kansa tace duk ranar da ka Kara sai naci ubanka matsiyaci,ta wullo shi waje tana cewa Allah yasa barayi su Kama ka,Jummai tace ba Ameen ba inshaallah sai Sallah zan yanka shi.. Akuyar Munnir ce tayi kuka meeee ....Mero tace kan Babarki munafuka uwarki za ayi miki ba an Baki abinci ba,ke a akuyoyin ma baki da kyau kumatu kuful kuful duk tayani Muni shegen Ido duk kwantsa,in Baki wasa ba sai na kaiki kasuwa gobe ta ja tsaki ta koma bedroom. Sai 2:30 Mero ta fita Inda take sana'arta tana cikin zubawa wani abinci a plate zai siya Haneef ya motarsa baka katuwa ta gangaro a hankali,Yana bayan mota ya hango Khadija cikin Maza tana zuba abinci,kishi ya kamashi Wanda bai taba Jin irinsa ba,sai da ya dandana Mero ma ya fara wani mahaukacin kishinta baya kauna wani ya kalleta. Yanzu Kuma bashi da bakin magana,driver yayiwa magana da ya tsaya,bayan sun tsaya ya fito ya Sha glass ga wani danyen yafi a jikinsa fari ba karamin kyau yayi ba,gaba daya kallo ya Koma kansa,ya tako a hankali Inda Khadija take hankalinsa duk a tashe,ko kunyar uban kowa bai ji ba yace Dan Allah kiyi hakuri, Bai kamata a shafe duka alkhairan mutum ba,ki tausaya min,Khadija ta kalle shi kawai ta ja tsaki taci gaba da zuba abincinta kamar bada ita yake ba,mutane suna jinsu,idan ba so kike na fadawa duniya ba Dan Allah kiyi magana,ba tare da ta kalle shi ba ta furta ka fa takura min kaje wajen wata mana dole ne ana so dole ne ta ja ta juya taci gaba da cinikinta. Idonsa ya lumshe zuciyarsa tana suya ya juya ya shiga mota abinsa sabo da Yan kauyen sai kallonsa suke yi,Yana shiga mota ya runtse idonsa tare da zuba tagumi hawaye suka zubo Masa na takaici,Driver ya sa suka juya kawai. Yana komawa gida ya samu Mamansa tazo ta neme shi a waya taji shuru,Yana shiga Parlo ya ganta,Mama tace Kai me ya sameka Subhannallah naga ka rame Haneef baka da lafiya ne,ko magana baiyi ba ya wuce ya haura sama abinsa ai duk sune suka ja Masa. Mama ta bishi sama kafin ta shiga ya sawa dakinsa key ,Mama mamaki ya kamata,Danta me biyayya bai taba yi mata haka ba,tace Haneef wai lafiya,kukansa taji kawai a ciki,tace na shiga uku ni Yar nan,ko akan Khadija ne? Wlh idan a kanta ne na yarda ka aure ta,na yarda Dan Allah kayi hakuri ka bude kofar,Haneef yaki budewa tana cewa Haneef nice fa na haifeka bani da kowa sai Kai Haneef,Haneef ya tashi ya bude sabo da darajar iyaye,hannayensa ta rike tace meke faruwa ne? Gefen bed suka zauna Yana hawaye sosai ya bata labarin abinda ya faru,yace kune kuka bata min rayuwa,kune Sila ai, Salati Mama ta dinga ja,tace me yasa baka fada min ba? Kince ko mene bazan aure ta ba,nayi nayi dake ya kike so nayi,akan Ihsan din da Bata damu dani ba,yanzu Khadijan taki hakura? Yace ae taki hakura naje naje har na gaji da zuwa tace baza ta aure ni ba,wlh idan bata aure ni ba sai na zama Dan iska cikakken,sai na koma goggen kati,ai kune kuka jawo min,Mana tace Inshaallah zata hakura kaji,yanzu kayi hakuri ka daina zuwa tukun sai ta huce Inshaallah zata hakura,yace to ai ni idan ban ganta ba bana Jin dadi sannan yanzu sana'a take yi a cikin Maza a samu a hanata kawai wlh. Mama tace ka daga kafa kayi hakuri shine dai dai Haneef,ka daure kaji,yace to zan gwada,Mama da kanta tayi girki yaci tana lallaba shi da kanta ta bashi a baki. Mero shuru taga Haneef ya daina zuwa,yau tana dakinta ta dawo daga sana'a tayi wanka ta kwanta tana hutawa,in banda tunanin Haneef ba abinda take faman yi sai tunanin Haneef,a fili tace aikin banza to kar yazo mana in bai zo ba sai me,na zauna Ina batawa kaina lokaci a banza ta ja tsaki tare da furta Ina ruwana da shi mtsswwww ta ja tsuka ta Mari kumatunta tare da furta ke dai Mero Tinkiya ce balama haba. Jummai tana kallon Yarta kullum a tunani take,tace Khadija kina son bawan Allah ki hakura ki aure shi,nasan Nima ban kyauta ba banyi aiki da hankali ba wlh Sam,yanzu tunda Sani ya rasu nake Jin Ina ma na dawo da rayuwa baya na gyara Halayena,Munnir Yana jinsu yace in an fada muku gaskiya ai bakwa ji sai da ta baci,duk uwar da ta sa son abin duniya a ranta wai yarta itace jarinta to tana da wahala,dama an haifi yara ne su zama jarin iyaye?,ace yarinya itace zata kawo kudi Kuma ke Inna Allah bai hana ba,Baffa Yana da rufin asiri kina sana'a amma kika yarda Yar da kika Haifa a cikinki itace jarinki,yanzu wa gari ya waya? Ina fada muku gaskiya baku ji,ai nasan boye min kuke yi amma naji komai Kuna zancen,an lalata Khadija,wannan izina ce abinda ya dace tuntuni ace anyi mata kenan dama ko Kya gane gaskiya Inna,Allah ya kiyaye ma ba da ciki kika ganta ba,yanzu ya rage naku ko ku gyara ko karku gyara,amma mace kamar Khadija a aikatau ai gwara tayi aure. Jummai shuru tayi,Munnir yace sai kiyi hakuri kaddara ta riga fata ki rufawa kanki asiri ki aure shi,domin wallahi wani ya aureki in ya gane zaki Sha gori da wulakanci,wa zaki samu ma kamar sa,gwara ma ki hakura kawai ku rufawa juna asiri. Khadija da Jummai shuru suka yi kowa da abinda yake tunani a ransa,suna ganin Munnir yaro amma ya fisu hangen nesa,Jummai tana Jin wani irin daci a ranta marar misali da irin abubuwan da take aikatawa, yayin da Maman Haneef ta zauna tana kula da danta sosai tana kwantar Masa da hankali. Spark Yana Office Yana meeting Naila ta addabe shi da kira,ya zaci wani mummunan Abu ne ya faru,ya dauki Excuse ya daga wayarsa yace family issue ne,Yana dagawa Naila tace Baby Yana son Ganinka ka dawo gida wlh,Murmushi yayi yace yaushe ya fada? tunda ka fita yake cewa Daddy ya dawo gida Kuma a siyo kifi ya kare kasan in baici kifi ba ulcer ce zata kamashi,yace ai zan dawo meeting fa nake yi,mu Ina ruwan mu da Meeting dinka in zaka dawo kawai ka dawo muma ai meeting din sai ayi damu,kudin da zan samu fa a barshi? Naila tace wlh in baka dawo ba sai nazo yanzu,yace zanzo kwantar da hankalinki Babyna,tace to sai ka dawo,Kuma yau kazanta nake ji ba Wanda zai Sa nayi wanka a gidan nan,yace ai normal dama turawa ma basa wanka kullum mune sarakan tsafta sai mu dinga wanka kullum ai watarana sai mu huta,tace we love you,ke da wa? Baby mana,I love you too Baby girl ya kashe wayar,Suna jinsa su mamaki suka yi bai tashi ba a gabansu yayi kalamansa ko kunya bai jiba,kowa idan zaiyi waya da mace fita yake amma Banda Spark ko a gaban uban waye maganarsa yake. Fuskewa yayi suka ci gaba,abinda Naila tace ya sa an Kai mata amma bai koma gida ba sai da ya tashi gaba daya,yasan akwai rigima Yana zuwa ya iske ta yanda ya fita ya barta kuwa bata yi wankan ba,yace Beb ba sannu da zuwa? Ashe Baki wankan ba? tace kazanta nake so yau haka zan kwana,tashi to muje gidan Arham,Arham Kuma? Ae mana sun tare ai,dubiya zamu je mu gano Jikin,Naila tace to amma Allah ni yau bana son wanka kazanta nake so ala dole zanyi,sai inyi miki ma sorry muje,ya lallabata da wayo suka yi wankan,ana wanka tana harararsa yace me nayi Kuma? Sai kallon cikina kake yi ka juya bayanka duk nayi Muni,sai bayan sun fito suka shirya sannan suka fita,an Kai Masa abinci Office shi yasa bai nema ba yanzu. Suna zuwa suka iske Mayu Misam da Rafeeq a gidan,Arham ne ya fito shi a dole me gida ya Sha wanka cikin gezna Yana bulbula kamshi,tun kafin yayi magana Misam yake dariya,ya basar kuwa harda cewa ga parlo na ku dawo can,sai kace wani me gidan kirki cewar spark,bayan sun koma cikin parlon iya su Maza su hudu Naila tana wajen Basma,Misam yace yaro an girma Kuma,Arham ya share zancen yace ya aiki,mun barshi a Office dubiya muka zo a fada mana halin da Amarya take,Arham yace tana nan ranga ranga,Spark yace wai Kai namiji ko?Arham sosai ma kuwa Kai ai nasan ko kirji baka iya tabawa ba, you no sabi handle booby,Misam ya fara dariya harda buga kafa ance Spark boobs Bai iya sarrafa shi ba,Rafeeq yace Amma baka da kunya Arham babban Yaya guda Spark,Kai da kake maganar kasan scissors? Misam yace ni fa? ai Kai Dan bariki ne ba a ja daku jikan Zeenatu kasan komai,kasan clockwise and Anti clockwise?ya Kalli Rafeeq,Rafeeq yace Ina zan sani sai irinku Yan zamani,zaku zo ku dameni ya Amarya ya Amarya ba abinda ban sani ba na iya komai,a jiin mace Kun San Reginal zone?kuzo na dinga koya muku darasi,Spark tagumi yayi kawai Yana kallon Arham,yace in banda ku yayin ma gaku Nan ne dai me zai kawo ku gidan kaninku yau,jiya an kawo Amarya yau kuzo daga Jin nayi abin bajinta,sai kace mata zaku koyi tsegumi,sai kuje ta bude muku kuga dinkin ai,Spark yace shike nan tunda haka kace da matan mu Dan uwarka ma zamuyi a Nan Dan Munji ka tare munzo ganin gida tunda haka kace baza sake zuwa ba,Ni na zo kuje ai kamata yayi ku bari na kawo muku ita gida ta gaida manyan yayye amma sai kuzo Kuma ni da nake so ta kasa hada Ido daku sabo da kunya,Spark yace a'a ta kalleni wlh ni ko bani da riga ba ruwana zata iya kallona bare Ido,dariya Arham yayi yace ai shike nan tunda baza ka karbi girman ba,yace na barwa Misam,Misam yace yi can da shi ku bawa Rafeeq,Rafeeq yace ni ko yanzu ta saki layi binta zanyi muyi zancen a barwa Khalil girmansa,Spark yace girma ai sai Papa su ya kama da Mummy na,Kai kaga Mummy na Kai mata ziyara ta dinga shagwaba,Allah sarki Baseeru Kusa ta tuna tayi zaton shine cewar Misam, Spark yace Inda kasan ta macen kwaduwa Ina da uwa a wajen nan,Mummy Bariki a jikinta yake,Rafeeq suna dariya,ta fashe min da kuka my son ana fari nace ahhhh...Misam yace Kai duk haka suke wlh har Mima har yanzu wai Papa Yana Jin dadin shagwabarta bai daina jiba,Rafeeq yace Kai Misam bama son sharri yace to haka na gani da idona na fuske kamar ban gani ba,Arham hankalinsa Yana kan Amarya shi Kam,yace wai kuwa in aka yi dinki suna yin sati basu warke ba? Tambayi masu jego cewar Misam,wayarsa ya dakko yace bari nayi searching a Google ya fara rubutawa da turanci yace Yan midwifery Kuna Ina kuzo ga ranar ku,akan haka sai na tafi asibiti nayi tambaya. Naila kuwa tana wajen Basma wacce ta dan zauna tare da jingina da Jikin bed,Naila tace Amarya an Sha Mai,Basma kamar zata yi kuka tace Allah bazan sake yarda ba kamar an tambayeta,taci gaba da cewa Dan kawai yace kar na fada ne ba kyau amma wlh da sai duniya taji abinda yayi min,dama ai ba sirri ne dani ba,bana barin zance a ciki ni,yanzu Yar maganar nan ta sirrin aure da aka hanani fada a kanta sai nayi muguwar rama sabo da zata dinga cina a rai,Naila tayi dariya tace ai Basma babu me tausaya miki ko kadan irin rashin kunyar da kuka yi. Ai na zaci mutumin kirki ne ashe ashe ba haka bane. Sun dade a haka suna Hira kafin Spark yace ta fito su tafi. Suna watsewa Maman Rafeeq ta zauna a dakin Basma ta kafa ta tsare,Arham yace nifa wlh ban San zance ba,gwara ki tafi kawai ko na tube a gabanki wlh ai uwata ce ke in kin kalla ma na danki ne,idan Kuma so kike to kema zan iya Dake,Mama tace na shiga uku na lalace Arham ni din kanwar uwarka,to ki canja daki Tabesting zanyi ko nayi a gabanki,Mama tace ba Inda zani karamin marar kunya,a gefen Basma ya zauna Yana kallonta Yana shafa gashinta yace Babyna Yaya? Kirjinta ya taba da hannu biyu ya rike ya sun daina ciwon? Mama mikewa tayi a gigice yace bude muga ciwo in Dan lashe miki....kafin ya rufe baki Mama ta tsinci kanta a waje tuni,dariya yayi Gani yanda ta bar dakin yace da ki zauna mana Kiga yanda akewa Nippi Nippi. Ayi hakuri Ina wajen sauka AsmaBaffa [3/4, 8:35 PM] AsmaBaffa: 🏫TANTIRIYA🏫 A GIDAN YARI BOOK 3 ~TAIMAKO~ 66-70 Official By AsmaBaffa SADAUKARWA NE GA AIDA MAMAN TASNIM page naki ne Amina Yusuf Bawale Haneef ya gaji shuru shuru har sati,mama ya samu a kitchen tana aiki yace Mama yau sati daya ban je ba ko ta huce yanzu? Ya dace naje ai na gani ko,Mama ta kalle shi in Bai je ba hankalinsa bazai kwanta ba tace jeka mana,Allah yasa ta huce din,yace Ameen tare da wucewa ciki zai shirya yaje,Mama Gani tayi ya fito cikin shadda Yar gaske Arsh,ya fesa kyau kamar wani ango Sabon aure,Mama ta kalle shi kawai tayi murmushi,ya furta zan tafi,to baza ka tsaya kaci abinci ba in kaje bata huce ba fa a Ina zaka ci? sai zumudi yake yi da kyar ya zauna ya dan ci abincin Yana sauri ya yiwa Mama sallama ya tafi driver ya ja suka wuce. Wurin 3pm suka Isa can Yana mota tana tafiya a hankali,Driver dinsa yaji Yana cewa wow dama a kauye akwai irin wannan,wow yarinyar dirinta yayi kaiiiiiiiii,Mero ce ta juya baya tana tafiya taci wanka cikin doguwar rigar atamfa me aljihu ta yafa siririn mayafi iya kafada hannayenta cikin Aljihu duka biyu,duwawukan Mero suna motsawa a ciki,Haneef Jin irin maganar driver ya Kalli gaban motar yana ganinta yasan Khadija ce,gaba daya haushi ne ya kamashi,wani kishi da bakin ciki ya taso Masa,yace driver Maza kaje saitin wannan yarinyar zanyi magana da ita,Kafin su karasa wani ya tare Khadija suka tsaya,Haneef ya tsaya da mota a saitinsu tare da sauke glass kasa,Kallo daya Khadija tayi masa ta Maida hankalinta wajen guy da ya tare ta,Mero ta furta Abdul Ina jinka,yaka kallon Mero kamar ya cinyeta yace Khadija na Dade Ina sonki a garin Nan,Haneef kunnensa ya Kara budewa yaji me Khadija zata ce,yace na Dade Ina kaunar ki Khadija,Dan Allah ki daure ki bani dama Khadija na turo gidan ku,wlh da gaske nake aurenki zanyi,nan take Mero tace Ina sonka nima,Kuma naga ka Dade kana so na Abdul tun Ina karama na amince ka turo zan aure ka,Haneef bai san sanda ya bude mota ya fito ba,Yana zuwa yace Khadija meke damunki? Mero ta Harare shi tace ta juya wajen Abdul tace ka turo gobe ko jibi tayi tafiyarta. Haneef a wajen ya tsaya kamar gunki ransa ya baci,idonsa ya canja kala,Nan take zazzabi ya fara lullube shi yaji wani jiri Yana daukansa yuuu yuuuu....mota ya koma ya shiga ya kwanta a bayan mota tare da rike kansa yace da driver juya mu koma gida kaini asibiti kawai,Driver ya fyalle mota da gudu sai birni suka wuce asibiti. Mero kuwa tun a hanya ta fara kuka tayi sauri ta fada gidan su tana zuwa ta shiga da kuka,Jummai ta gama tace awararta ta saka a faranti zata fara yankawa Mero ta shugo tabi ta kan awarar da takalmi ta taketa tace wlh yau baza ayi ciniki ba,kowa bazai zo siyen awara ba ta wuce cikin daki ta zuge jakar kayanta ta zazzage su a kasa ta fada Saman katifarta ta hau rusa kuka tana wayyoooo Haneef Ina sonkaaaaa......Allah ka Gani Ina sonsa,sai shiga Raina yake kullum.....Jummai ta fita unguwa ta dawo ta samu Mero tana kuka ga awararta kaca kaca a faranti,tace Khadija kece kika min barna haka ko kuwa wani mugun ne daga shiga makwafta in dawo shine kika yi min haka,sabo da baki da mutunci,wallahi wallahi ko ki yarda ko karki yarda Haneef Yana zuwa zansa ya Kai kudin aurenki wajen iyayenki Maza tunda Yana sonki,Khadija tace ni Abdul zan aura nace ma ya turo gobe ko jibi. Wanne Abdul din? Abdul na gidan Magaji wanzami?Mero tace ae shi,Jummai tace idan kin aure shi Allah ya tsine min Khadija,wlh gwara na mutu,wannan Dan shaye shayen? ga talauci da me zai ci dake da wacce sana'ar? Bashi da sana'a fa,wannan kazamin ma in banda doyi me Abdul zaiyi,ki aure shi ai Kya Sha doyi kuwa,ga me kamshi Haneef wannan kamshin kadai in kina shaka a turaka Rahma ce da Ni'ima,wlh ko ni da zan iya Maida kaina budurwa da na mayar na kwace Haneef din ni ya aure ni,Mero tace a gidan nan wacce kazantar ce ba a ayi, kazanta iri iri badan yanzu ba da nake gyarawa nidai bazan auri Wanda ya lalatani ya cuce ni ba,to zanga wacce zata yarda ki aure Abdulfata din. Abdul fata kuwa tunda Mero tace ya turo bashi da ko sisi na sigari ma ya gagare shi,ya rasa Inda zai sa kansa,akuyar Tinkiya guda biyu na babansa ya sace cikin dare ya kaisu gidan abokinsa ya ajiye washe gari zasu kai su kasuwa. Haneef ana wucewa da shi asibiti ya kasa tashi ya fito da kafafunsa sai driver da wasu daga cikin asibitin ma'aikata aka fito da shi tare da Kai shi ciki,Driver Mama ya kira tana zaune tunda Taga kiran driver ta firgita,ta daga yace Mama muna asibiti wlh munje unguwar to ya hadu da yarinyar da yake zuwa wajenta kawai ya ganta da wani saurayin suna zance to sai ta bawa waccen saurayin dama ya Kai kudin aurenta zata aure shi,daga nan ya dawo mota tun a mota yace na kaishi asibiti,wlh muna zuwa ya kasa fitowa da kansa sai shigar shi aka yi,Yana nan ana bashi kulawa,Mama tace wanne asibitin kuke? Global health clinic,Gani Nan cewar Mama,hankalinta a tashe ta nufi asibiti. Zuwanta ke da wuya ta samu Likita ya fito Yana cewa zaku iya shiga kuga Jikin shock ya samu saura kadan zuciyarsa ta samu matsala amma Allah ya kiyaye,Mama ta shiga tana salati,Haneef ta samu a kwance Yana bacci ta hau kuka a hankali sabo da kar ta tashe shi,Driver ta samu tace Dan Allah kula da shi dole na tafi gidan su Khadija bani address,Driver yace mama ki bari yamma tayi,Mama tace a'a kyale ni yaron nan shi kadai na Haifa duk duniya bani da kamarsa Allah ne gatana shine gatana,Driver ya bata number kuwa ta tafi garin,Bata Isa can ba sai da magriba,da tambaya aka nuna mata gidan su Khadija ta shiga,lokacin Khadija bata nan ta tafi gidan Yan uwan Mahaifinta. Jummai tana ganin Mama taga suna yanayi da Haneef,hannu bibiyu ta karbeta a dakinta ta kawo mata ruwa da tuwon daren data kwashe,Mama Sallah ta fara gabatarwa sannan tace nasan baki sanni ba,ai nice mahaifiyar Haneef,Jummai tace ai kuwa naga kamanni, nasan kin San mene ne ya faru tsakanin Khadija da Haneef,kaddarar data fada musu,wlh sharrin shedan ne,Dan Allah ku yafe masa,Khadija nazo na bawa hakuri tayi hakuri ta yafe Masa Dan Allah,tace a sanadin wannan abin Haneef yana kwance a asibiti,Mero ce ta shugo gidan ta tsinci Mama tana cewa Haneef yazo ya samu Khadija tace wani ya turo wlh bai koma gida da lafiya ba sai asibiti aka kaishi Yana can bai San Ina yake ba,zuciyarsa ce ta samu shock saura kadan ta samu matsala Allah ya tsare,Dan Allah kuyi hakuri ku yafe Masa,Sallama Khadija tayi kamar bata ji zancen ba amma hankalinta a tashe yake. Ciki ta shiga tace laaa Mama kece? Mama taji dadin yanda Khadija ta mata tace nice Khadija nazo baki hakuri har gida,Dan Allah ki yafewa Haneef,Khadija ta furta ai na yafe Masa ni tuni,Mama taji dadi tace na gode, Dan Allah ki aure shi Khadija,Mero tace ai ni wani nake so Mama,Dan Allah yayi hakuri,Jummai tace Kinga Maman Haneef na bashi ita rabu da ita,a kawo kudin aure wlh ko a gobe a daura indai kun kawo kudin aure da sadaki a ranar za a daura,Khadija zata yi magana Jummai tace kina magana wlh sai mun raba gari,Shuru Khadija tayi ta tashi ta fice,Mama tace kar ayi mata dole dan Allah,Kyaleta karya take tana sonsa wlh cewar Jummai,suka gama Kus Kus dinsu da Maman Haneef sannan taci tuwon kadan tace ta koshi a daren ta samu me taxi dan garin ya kawota birni drop. Asibitin ta koma ta samu Haneef a zaune Yana cin Ayaba,farin ciki tayi ta zauna a gefensa tana tambayarsa ya jikin? yace da sauki,Yana cin Ayaba Yana Jan tsaki shi kadai,Mama tace Haneef ka kwantar da hankalinka Inshaallah gobe sai an daura Maka aure da Khadija,Haneef yasan ma bazai yuwu ba,yace hmm kawai Allah ya kaimu,ka shirya gobe da kawunka zasu zo har abokinka Isma'il ka gayyato tunda Kai naga baka fiye abokai ba,Haneef ya kalleta kawai dan bai San taje garin ba ma Kuma bata fada Masa ba. Washe gari da safe aka sallame su Mama ta damu sai Haneef yayi shiri,cikin sababbin kayansa ya saka wata tsadajiiyar shadda fara kar,bai sa hula ba tace ai dole sai ya saka,haka ya saka ya shirya sosai ya fito a angonsa,jikinsa a sanyaye yasan tatsuniya ce,ita kuwa Mama har ta fara Shirin hada Lefen ma,Su Kawu su biyar suka iso daga Adamawa suka tafi a mota biyu har abokin Haneef Isma'il suka tafi garin su Khadija,Munnir shi ya raka su har gidan dangin Sani ubansu Wanda Jummai taje ta fada Masa Khadija ta samu miji na kirki amma taki yarda,ita ta gaji da girman Khadija a gida,zasu kawo kudin aure da sadaki kawai a daura aure. Yace ai dama kune kuke kyaleta duk garin Nan babu sa'an Khadija Allah ya kaimu za a daura indai kin gamsu da tarbiyyarsa da Halayensa da gidan da ya taso ba matsala,Jummai tace na gamsu,sun San masifar Jummai sannan sun gaji da ganin Khadija taki aure a kauye ko wacce ana mata aure banda ita,Yan uwa ya fadawa,kowa yaji sai murna za a aurar da Khadija a daina musu gori a gari. Washe gari tun kafin suga angwaye suka Tara mutane a masallaci ana jira,Munnir yasa Yar wankakkiyar shaddarsa ya rakasu masallacin,Haneef ji yayi kawai ana cewa ga angwaye sunzo,mamaki ya kamashi dan bai zaton hakan ba,su Kawunsa ne akan komai sune suka Bada dubu Dari biyu kudin aure sannan Kuma aka Bada sadaki dubu dari biyu Shima,Dangin Khadija suka ce yayi tsada gaskiya su a rage,Haneef yace baza a rage mata ba ai sunyi ma kadan,Isma'il Yana ta mamakin auren Haneef haka Emergency,Nan take Liman yayi Khuduba mutane suka sheda aka daura auren Khadija Sani da Haneef. Ana gamawa Haneef yaji hankalinsa ya kwanta nutsuwa ta zo Masa,wani irin farin ciki da nishadi ne suka lullube shi,ji yayi a duniya Kam baida Matsala shi dai,yace Anya kuwa da gaske ne ba mafarki nake ba? Isma'il yace da gaske ne duk mun sheda sai mu tafi gida sai an kawo Amarya,Haneef yace ni a nan zan yini kabi su Kawu ku tafi driver na muna tare, Isma'il ya zaro ido amma Haneef shi ba komai Aboki ke sani nasa ba shi yasa Isma'il bai San komai ba akan Haneef sai kadan. Su Kawu yabi suka tafi Haneef da driver dinsa suka je gidan Khadija,yaga ana ta shiga Allah Sanya Alkhairi yace ashe dai da gaske ne,yaro ya tura gidan yace a kira Khadija inji Angonta,Khadija tana ta kuka an daura aurenta da Haneef,tana daki ta boye kanta,itama Jummai bata nunawa mutane ita,Yaro ne ya shugo yace Khadija tazo inji Angonta Jummai tace kace gata nan,da kanta ta shiga dakin Khadija tace tashi ko na ci ubanki,Kuma wlh in Baki je ba Khadija sai na tsine miki ki tashi kije tun wuri saura ki Masa fitsara,Khadija ta tashi tana hawaye,wanka ma da kyar tayi,taki yin kwalliya ta zauna daga ita sai vest da skert na atamfa,Hijab Jilbab ta dauka har kasa dogo me hannu ta saka tana goge hawayenta Wanda ya kasa daina zuba. Yana ganin ta fito ya sallami driver yace zan kira ka,Driver ya Kalli Khadija yace ki shiga bayan mota Yana ciki,maganar mahaifiyarta ta tuna dole ta bude motar cikin fushi ta shiga ta zauna bata Kalli Inda yake ba ta sake fashewa da kuka,Haneef ko a jikinsa shi hankali kwance,yayi murmushi tare da riko hannunta,da sauri tasa hannu ta make Masa hannu ya saki ba shiri,yace kiyi hakuri Khadija,ba laifina bane na miki dole ki aure ni, Dan Allah kiyi hakuri ya kwantar da kansa a kafadarta ta janye jikinta da sauri tana harararsa,Kyaleta yayi yace zan tafi,mota ta bude fuuuuuu ta shige gida abinta,driver ya kira suka wuce,sai bayan ya koma gida Mama ta bashi labarin yanda aka yi har aka daura Masa auren da Khadija. Godiya ya shiga yiwa mahaifiyarsa,Mama tace to sati me zuwa za a kawo ta sai kabi komai a hankali har ta huce Nima yau zan koma gidan mijina sai munzo kawo lefe,yace mama akwai kalar kayan da nake so zan saka da Kuma dinki,ai dama komai na bar Maka ka siya da kanka abinda naga zan iya ko ya kamata zan tuna Maka yace to na gode.yau Haneef sabo da murna har da zuwa wajen abokansa ya Kai musu ziyara,Jummai Kam ta aurar da yarinya murna kawai take abinta tace in da rai sai a Ganni watarana a saudiyya ko a Ganni da yarona Munnir mun koma birni,duk Wanda ya shugo sai ta Masa zancen Inda rai da rabo sai a jini a saudiyya ko mun koma birni ma gaba daya. Yan hassada sai tsinewa Jummai suke uwar son kudi wai Dan me kudi ya auri yarta wai zata tafi Makkah ko ta koma birni,ana ta zuzuta auren Khadija yanda tayi tsada a kauyen. Abdul ya saci tinkiyoyin ubansa ya Kai kasuwa Yana dawowa da kudinsa zai Kai na aure yaji an daura auren Khadijansa da wani,Abdul takaici ya kamashi yace wlh sai dai in Khadija baza ta fito ba sai ya nada mata duka yayi mata tsirara a cikin mutane,Bai San Jummai ta Hana Khadija fita ba wai gyarata take yi,kullum sai ya tare hanya ko zaiga Khadija amma ba labari. Kudin auren Khadija a ciki ake mata gyaran Jikin skin ne kawai ba a gyara ba sai taje birni. Munnir yace na Dade da gama secondary nasan ma kwana Nan zan koma birni mijin Khadija ya sani a makaranta sannan zan zama Dan gayu Nima ya bani aikin yi itama Inna a dauke ta mu bar kauye jaraba sarakan hassada da gulma,Jummai tace Allahumma Ameen Allah ya amsa maganarka,yo ai ni nayi farar haihuwa da abani na haifi Dan Majalisar tarayya ai gwara da na haifo Khadija yanzu zaka ga tausayi da taimakon iyaye da Yan uwa,Mero sai da tayi dariya yanda gaba daya suka Dora samun arzikin su a kanta,Munnir yace shi yasa nayi ruwa nayi tsaki akan auren nan sabo da ni Inna na hango ci gabana,Inna tace kwana Nan Munnir ko a hanya aka bani awara bazan kalle ta ba bare ma naci to ballatana Kuma ace nayi ta siyarwa,to mun koma birni ma Ina zanyi awara na dai siyar da wani abin amma Banda awara. Mero tana zaune tana jinsu tana dariya sai da suka gama tace to wannan baida Imani baya kyauta Kuma baida tausayi in zaku cire rai ma ku cire,baza mu cire ba wlh cewar Jummai. Mima tana zaune Mufee sai waya take tana Kus Kus Kus waya ba dare ba rana da Haidar,Mima tace Kinga nifa na gaji da wannan abin wlh zan sanarwa papanku kawai Haidar ya kawo kudi bazan iya wannan masifar taki ba Mufee,ke a duniya baki da aiki sai waya,Shaheed da Junior suna zaune,Shaheed yace uhm ai gwara ayi mata auren,kina dai ji har kalan kayan da tasa ta fada Masa wlh idan pant ne a jikinta fada zata yi tace pant ne a jikinta red da bra,Yana jin haka me yayi saura sai wani abu ya darsu a ransa daga nan sai a fara zancen iskanci,Junior yana jinsu yace tab rannan ma kalar kayan bacci ta fada Masa,harda cewa bata Sa masu nauyi Ina jinta,Mima tace ya turo kawai ni wlh na gaji,yara kamar zasu kashe ni kowa da kalarsa,Maman Rafeeq ce ta dawo sai Ganinta suka yi afjajan,Mima tace ya haka ke da kika ce sai sati yau da safe a ganki kin dawo,tace uhmmm kema kin sani ai wlh ni Kam bazan sake zuwa gidan Arham ba,iskanci a gabana da kalaman banza,na fito na dawo parlo ya dakko Amaryarsa a hannu ya dawo parlon da ita wai gidansa ne baza a hanashi shanawa ba duk Inda yaga dama a nan zai kwanta da matarsa,ya dawo parlon wai a nan zasu huta,Mima tace ke wayo ya miki ya Kore ki fa" ke Kuma sai ki taho,ki nuna Masa Yar zamani ce banza sokuwa sai ki taho,Maman Rafeeq tace a'a Dan duniya ne wannan wlh baku ga abinda yake ba a gabana yake taba ta,Junior yayi dariya yace ai kune ku kyale shi sai ta ginshe shi kuka wani tafi,Mima tace wace zata ginshe shi? badai Jinina ba,Khalil ya riga kowa aure amma har yau mace bata isarsa bare Arham, dan Allah ku kyale su mana cewar Junior, Shaheed yace ku fadawa Spark ya bashi shawara watakil ya gyara,Mima tace ai Arham yace Spark ma bai iya yiwa matarsa komai ta Ina zai bashi shawara ya yarda,tsokanar su yayi kawai amma zaiji indai man to man ne,Mima tace wato mu ya raina mu ai shike nan. Mima ta tambaya to ya Basma din? tana nan itama bankadaddiya shuru take bata korafi sai yanda yayi da ita cewar Maman Rafeeq,Mima tashi tayi ta shiga daki tare da kiran Spark,bugu biyu ya dauka tana Jin Naila ta ciki tana kuka,tace Kai naji kamar kuka?Spark yace sirikarki ce da jikanki suke kuka,Jikanki ne yace tayi kuka,ni na taba ganin ciki haka kullum sai anyi kuka,Spark yace Ina ganin ta kaina Mima,danki Yana Jin jiki a rayuwa,Jikanki Yana abinda yake so,Naila ce tayi dariya tana goge hawayenta,Mima tace maganinku dama irin wannan cikin ai a saku a gaba shine dai dai,Spark yace Kuma Baki San tsiyar ba bana iya ko yi mata fada bana iya tsinana komai sai dai na lallabata,Mima tace to tsoronta kake ji ai wani iskancin ma na mata ai sai ana biye musu suke yinsa,Spark yace uhm uhm baza ki ja min salala n arziki ba,Mima tace kace kawai salalan tsiya yafi,murmushi yayi yace Baby ga Mima ya mikawa Naila waya ta karba suka gaisa da Muka tace ya jikin? Naila tace kalau nake Mima Alhmdllh,Spark yace Ina fa kalau ga me ciki. Sai da suka gaisa sannan ya karbi wayar Mima tace Dan Allah Arham zaka yiwa fada ya kula da matar nan kar ya kashe musu Yar mutane mu shiga uku,sannan ka dinga Kai Naila tana bata shawara tana dorata akan layi,Spark yace Arham yafi karfina kina Gani yace ban iya komai ba cikin matar tawa ma rabo ne yasa aka samu,Mima tayi dariya karka Kara Masa sharri Spark to haka yake nufi mana tunda ba wata uwa na iya tsinanawa ba Kinga kuwa ai rabo ne kawai yasa,to ayi hakuri ai wasa ne,Ina Jin dadi Ina murna kanku a hade Kun hade kanku Kun zama abokan juna,matan ma haka nake fata su kasance dan Allah ku kokarta,Spark yace to zan gwada tace yawwa ta kashe wayar. A ranar Spark ya fita da mota har kofar gidan Arham ya Masa waya ya fito,Yana fitowa yace idan aike ne nifa bazan je ba Ina da aikin yi,Spark ya bata rai ba wasa yace shugo mota Dan Allah karka bata min lokaci,budewa yayi ya shiga gaban mota,Spark ba alamar wasa a fuskarsa,Arham ya kalle shi ba mutunci yau,yace yau Allurar ce ta motsa? kaga Raina a bace yake wlh ka kyale ni kawai bana son wasa,yanzu Kai Arham haka ake yiwa Amarya? Dan Allah ka kyale ta a samu ta warke karka cutar da ita,Arham yace wai ni da matata Azo ana bani doka,in ka lalata ta har ta fara yoyon fitsari ai Kai ka sani,Baki Arham ya bude yace yoyon fitsari? Abin har ya Kai haka? Spark yace kwarai ka tambayi likitoci shi yasa muke jiye Maka tsoron hakan Dan ya tsoratar da shi ya fada masa,kar a cutar da yarinya,Amana ce fa,mudai muna fada Maka gaskiya ka barta ta warke idan ba haka ba Kai ka jiyo ko me ya faru,Arham yace tab Kai fa naga ai ba kyale Naila kayi ba,har kana da bakin magana yarinya har kuka take a gabanmu idan ka dawo,sai ni daga an samu matsala,ai Naila ta girmi Basma,Arham yace da Shekara nawa? Nailan yarinya ce fa a gidanka ma ta Kara girma ai ko zata girmi Basma sai dai da Shekara daya ko biyu,Nailan da take kanwar kanwata.... Spark yayi murmushi yace wai yaushe ka fara son Basma din? Kace baka sonta? Na canja to Ina sonta yanzu ba shike nan ba,Ina son abata Kuma inshaallah zata warke da wuri,Spark yace baka ji ba kenan? akan me zanji tunda Allah yace gona ce mu shiga ta Inda muka ga dama,ai shine na shiga ta Inda naga damar, ni bazanyi noma a layi layi ba wlh,idan na faro ta gefen yamma,sai na tsallaka kudu,na dawo arewa a haka zanyi ba wani a layi,Spark yayi dariya sosai yace to shike nan in ta fara yoyon fitsari yace nayi a haka Ina so,Spark yace Allah ya taimaka,yace Ameen ya ma taimake ni,Naila zata zo anjima,kar tazo ta ziga min mata muna zaune lafiya Ina mata wayo tazo ta ziga min ita amma dai ai Aunty Naila ce tazo,da matar Rafeeq ce ko Chika bazan yarda ba,Chika fa chiki ya tsufa haihuwa ko yau ko gobe Kuma,Spark yace ai kuwa saura kadan,jeka ni zan wuce,Arham ya fita ya Masa Sallama ya koma ciki. Mima abinci ta shirya aka Kai gidan Arham. Basma tana zaune me gidan Arham ya shugo,kunyarsa take ji yanzu ita Kam,Bata so ma su hada ido,kallonta yayi suka hada Ido da sauri ta janye idonta,yace shike nan an daina kallona ma bare muyi Hira,ga chewgum Ina ci zan dawo dan barikinki fa, dariya tayi kadan ta kalle shi tare furta to ci mu gani chewgum din,a gefenta ya zauna ya dawo da Kafafunta Saman cinyarsa Ya fara mata tausa, ana lallaba Basma ga chewgum ana ci tana ganin Dan barikin ta, harda cewa baza ki Dade ba zaki koma school so nake PHD kiyi Inshaallah,Basma taji dadi tace na gode Allah ya Kara budi,Arham ya furta ke zan yiwa godiya da kika bani shashshaka da mai,dariya ta kama Basma tace nidai ba ruwana Allah,motarki tana Nan anjima zan are ta na fita,tace na baka aro ka dauka,tace ai ka bani ma kudin accnt dinka haka kace harda kudin Dake accnt dinka duka,Arham yace kaiii yaushe? Wannan baram baramar ko da wasa bazan yi ta ba,Basma ta saka jaraba tace wlh an Bata sai ya mata transfer ko ta kai kara wajen Mima,Arham yace to in an baki kudin da me za a ciyar dake,ko baki nayi ai baza ki karba ba na sani kina da hankali,Basma tace ni bani da hankali wlh sai ka bani kudina mota dai ka dinga aro amma banda kudi sai ka bani,kin yarda baki da hankalin ke? Basma ta furta ae dama bani dashi ni bana ma fata nayi hankali kawai ka bani kudina da kayi min alkawari,ta fara fushi akan kudinta,Arham tashi yayi yace Banga ta zama ba ya shiga kitchen ya buya sannan ya kira Spark yaji wuya yace ya Banga Aunty Naila bane har yanzu? tayi tazo mana,Kai fa kace kar tazo,Dan Allah tazo,ai zata zo na kaita school zata yi signing wasu takardu jibi zata fara lecture na gaji da masifar Nan ta cikin Naila gwara ta zama Busy,wannan zaman da take a gida tana hutawa taci ta Sha shine yake sata wata tabarar. Sai da suka dawo ya sauke Naila a gidan Arham ya wuce,tana shiga Basma tace Oyoyo ga Aunty Me darasin aure ,ke fa sai kace dillaliya haka kike, Basma wai wani Aunty me darasin aure. Basma tace wlh ki fada Masa ya bani kudina da ya min alkawarin ranar first night yace ya bani duka kudinsa na accnt yanzu Kuma wai ya canja,ni nace yayi min alkawari,motarsa ma yace ya bani zai dinga aronta a hannuna amma ita mota nace ya dinga aro ai sai ya bani kudin ko. Naila tayi dariya tace ke shashasha ce ai wannan wasa ne,dadinki ne yasa ya fada Kinga ya zauce kenan ai sai kiyi murna a kanki ana Sambatu,ko baki yayi ai sai kice ya barshi kawai tunda kin San dalili,Basma tace Ohhh Nan dama dadi ne yasa? Naila tace ae kema in kika fara Jin dadi haka zaki Masa kyautar baki sani ba,ai ni har gidan Abbana nace na bawa Spark,Basma tayi dariya tace tab Inama Abba zai ji kin Masa kyauta da gida,Naila tace ai bazai ji ba ma,Nifa gaskiya da naga Arham yanda ya susuce Allah na zaci aljanun ruwan maliya ne gaba daya a kansa,tunanina Yana da Aljanu masu yawan gaske cewar Basma,Naila tana dariya da wasa da dabara ta dinga Dan ganar da Basma tana koya mata abubuwa. Abba ne ya fito da tabarma waje kofar gida sabo da irin mugun zafin da ake ya shimfida ya kwanta Yana Shan iska a gindin bishiya yace kaiiiii...Abu marar kyau ma Yana da ranarsa,Zafi ma da ranarsa,ba iya su Mohsin dina bane suke waje,Nima gashi duk tsiya cewa zanyi Ina waje,Mohsin ana can ana labbaika kana kiransa zai ce ai Yana waje Yana kasar waje,duk Wanda suke wata kasar zasu ce Ina waje,Nima gashi duk uban da ya kirani Ina waje Nima, ko ta wannan bangaren ai zafi yayi amfani,Beauty ce ta fito yanzu saura kwana biyar tayi arba'in,ana sa rai da dawowar mijinta shi yasa take ta faman gyara jikinta,Abba yace Ina zaki je Kuma? Kullum sai kin fita wai Ina kike zuwa ne haka? Beauty tace Abba gyaran jiki nake zuwa fa,yace au to jeki a dawo lafiya,tana tafiya Abba yace ana jiran miji kenan Kai yaran zamani karku kashe irin su Jauro da gyaran jiki,Jauro ne kuke birge shi. Yana haka sai ga wayar Jauro ta shugo,ya daga yace dan halak kaki ambato yanzu nayi gulmarka ni da zuciyata,munci namanka,Jauro yace ai sana'arka ce kana Ina yanzu kana gida? Abba yace a'a bana gida wlh Ina waje na fita waje,Jauro yace ban gane ba kasar ka bari ga number dinka tana shiga,Abba yace Ina waje mana kazo ka ganni Dan Kaine kawai zan fada Maka gaskiya amma Ina waje wlh nima,Jauro yayi dariya ya kashe wayar kawai ya nufo wajen Abba dolo suka Sha hira. Washe gari Abba da rana ya shiga gidansa cin abinci ya iske Beauty ta hada gumi kamar me ana masifar zafi,yace ke kuwa Beauty sai kace kin fada Swimming pool ko kin fada teku,Beauty tace Abba fanka din ma zafi take hurowa baku da ac bari ya dawo a sa muku AC gaskiya zafin yayi yawa,Abba yace a sa mana har a kitchen sabo da watarana in na shiga taya Yar Inna girki Kinga na huta da hucin gas. Beauty tace duk za a sa,Abba yace har tabbaci kike bayarwa wato dai ta tabbata kin mallake Mohsin dina Kuma sai abinda kika ce,Beauty tayi murmushi,yace Ina sa rai shi zaiyi mata biyu Ashe mu zuriar mu sai mata daya,Allah yasa Aslam in ya girma shi ya rama min. Babar Iman tuni ta tare a gidan sahibinta suna cin duniyarsu da tsinke ita da Sudan,amma hankalinsa yaki kwanciya sai bikon Maman Rafeeq yake zuwa yi sabo da ya samu ya gyara kuskurensa,da kyar Papa da dangi suka shiga maganar aka sasanta itama Maman Rafeeq ta koma gidan part din kowa daban, Maman Iman taji dadin Hakan Kuma tana bata girmanta. Kudin Auren Haidar aka Kai Papa yace a kaiwa Spark,Spark ya kira Papa a waya yace ko haihuwa banyi ba ni gaskiya baza a dora min girma da wuri ba a kaiwa Yan uwanka ka fada musu su Kai can,Naila tace yawwa kana karba shike nan ka tsufa ko Da bamu ajiye ba,furfura ce zata feso Maka da wuri in kana shiga irin wannan sabgar ta manya,Papa Yana jinta ta waya,yace wato matarka ce ta ziga ka ko? Ince kayi Abu kace baza kayi ba,ba ruwanta papa jikanka ne yace kar babansa ya tsufa,Mamansa ya fadawa suka yi communication suka tattauna sannan suka fada min muka yanke shawara,Papa yace ka gama Karyarka ai tunda ba a gabana kuka girma ba ai Kuma sai ta Allah ni,Allah ya shirye ku ya kashe wayar ya kira ya basu address wajen Yan uwansa suka Kai kudi aka yanke rana wata daya tal. Hidaya kuwa bata da lafiya ta samu ciki sai amai take Shekewa kawai ko me taci amai amai kamar me,tana Amai Iman ma tana nata gasu makwaftan juna sunyi anko sai su hadu suyi ta tattaunawa,Hidaya taje gidan Iman tace ke ashe ciki ne dani,na zaci malaria ce ashe babbar malaria na dauka,ana zuwa asibiti wai ciki,shi kuwa murna yake fa kamar me,ni Gani nayi nayi saurin dauka,Iman tace kin hadu da mugun sauro wlh nima sauron shi ya cijeni,mijina likitane Ina samu tun kafin na fara laulayi ya fada min ashe da gaske yake inda kisan maye,Hidaya tace har ga Allah bana son cikin nan da wuri haka,Iman tace Ina so ni murna nake wlh,ai ni da shi so muke. Ihsan tunda ta samu gidanta ta kama me tsada Yan uwanta suka sata gaba basu yarda ba sai dai ta dawo gida tayi Idda a gabansu,ba yanda ta iya haka ta koma Adamawa ta dole ma saurayinta me kurkura Bai sani ba ta fada Masa a waya ta tafi Adamawa,Bai san tana da aure an sake ba ma Sam,suna waya sosai kusan kullum ne sai tura Masa kudi take kamar me. Mero kuwa ta Sha gyara wajen Jummai,saura Kwana biyu akai Mero gidan mijinta Yan uwan Haneef Maza suka kawo Lefe akwati Sha biyar set uku,an zuba kayan masu tsadar gaske kamar banza,Kauyen sai tururuwa ake ta zuwa kallon kayan Lefen Khadija Maza da mata yara da Yan mata,Jummai ana ta alfahari ana Jin dadi,Jummai ta fashe da kuka tace oh Inama uban Yar nan yana nan yaga duniya,Kai jama'a mutuwa me Yankan kauna Kai rayuwa abar tsoro ce,Sani ya tafi ya barni ni kadai har abada na gama farin ciki tana hawaye ta yagi cinyar kaza tana ci wacce tayi ragowa ta saukar baki,tace bazan sake nishadi ba a duniya,murmushi ko dariya in aka ga nayi a dole nake yinsa ba yanda zanyi ne,Wasu mata suka shigo suna guda suna duba Lefe,Jummai bata San sanda ta washe baki ba tana dariya tare da furta Alhmdllh yarinya ta tayi goshi. Kwana uku na cika Haneef da yamma ya tura motoci harda danginsa mata guda uku Yan dakko Amarya,gidansa ya Sha gyara an canja furniture da komai na gidan an canja shi,ya Sha gyara sai kamshi yake ta ko Ina ga Salamatu ta dawo bakin aikinta. Amarya tayi kyau sai haushi take ji tace wlh sai ya gane kurensa in naje gidansa zamuga matar da zai taba,ta shirya ta zuba kyau cikin kayan lefe ta sanya dakakken Leshi blueberry ,abin ba a cewa komai,Maman Haneef tana gidan tana jira a kawo Amarya tayi musu nasiha su wuce Adamawa,Jummai tasa Mero gaba tana ta lallashinta tana mata fadan aure,tace idan kinwa kanki gata kin zauna lafiya ke kika sani idan kin watsar wlh kinwa kanki Khadija kafin kowa ya shiga damuwa kece zaki shiga,ki zauna ki rike aurenki ki rike mijinki,kiyiwa Allah biyayya ki yiwa mijinki,aka yi hakuri da wasu ma banzaye ga wulakanci,ga fasikanci,shaye shaye,barayi sannan ga talauci amma matayensu suna hakuri da su bare mijinki,in zaki nutsu ma ki nutsu, ke har wata ce,wacece ke Kalli gidanku fa na gado,ba abinda aka mutu aka bar muku,baku da gata sai Allah. Sai da ta gama tace Allah ya bada zaman lafiya,Allah ya kade fitina sai nazo gidan ganin gida kuje Allah ya bada sa'a,aka fita da Khadija ana guda motoci biyar amma sabo da hassadar karamin gari da mata suka ki zuwa,wai su birni tayi Nisa baza su je ba aje aki dawowa da su,sai iya mota uku aka cika aka tafi,Wanda suke mutunci da Khadija Yan mata ne mutum biyu ne rak Rahina da Shamsiyya sune kawai. Gida ya bawa kowa mamaki yanda duk Yan kauyen suke zato ya zarta haka,bayan sun shigar da ita basu dade ba aka kwashe su da abinci ruwa da lemo carton carton aka zuba musu a mota aka Maida su kauye,Mama ta zauna daga Yan uwanta mutum uku sai ita suka yiwa Khadija Nasiha sosai sannan suka shirya tafiya gaf da magriba suka tafi Adamawa,Mama a waya ta fadawa Haneef sai Khadija kawai a gida sai Salamatu me aiki. Bai nufi gidan ba sai 9pm sabo da yasan Khadija ba kulashi zata yi ba shi yasa ma shi dai tunda ta zama tasa an gama Masa komai kawai. Khadija Kuma ko kuka bata yi ba Sam Sam. Tace me nake jira ma Haneef har wani ango ne na kirki da zan rufe Masa fuska sai ya bude" ta fitowarta Parlo ta hakimce tare da kunna Kallo abinta. Masu Sharhi Ina godiya AsmaBaffa [3/6, 3:46 PM] AsmaBaffa: 🏫TANTIRIYA🏫 A GIDAN YARI BOOK 3 ~TAIMAKO~ 71-75 Official By AsmaBaffa SADAUKARWA NE GA AIDA MAMAN TASNIM PAGE NAKI NE Mmn Zee Haneef ne yayi Sallama tare da shigowa dauke da Leda katuwa a hannunsa,Ganinta a parlo ya sashi farin ciki da nishadi a zuciyarsa,baya so ya sameta tana kuka dama,da kyar ta amsa sallamar,a gefenta ya zauna ta matsa da sauri gefe,tace hmm me kike matsawa na riga nasan komai naki fa? Khadija wani haushi ya kamata ta kumbura,ya kalleta yayi murmushi dama tsokanarta yayi yace ke bakya tuna ranar dan Allah baki ji dadi ba?,takaici ya kama Khadija ta mike zata bar parlon ya fisgo ta tare da bata rai ba wasa,Bata taba ganin bacin ransa ba sai yau,yace Ina magana zaki tashi sa'anki ne ni,Ina mijinki Ina magana and you are walking out of me,wai tunaninki jikinki na damu da shi? ki rike abinki indai Haneef ne bai Kara zuwa ya nema,me zaka ce ka riga ka nema ai dai kaji kunya tunda ka iya fyade,nifa bari kaji ba wani muzurai da zaka min bari in fada maka Kaga a kasar nan kowa Yana da degree"kowa akwai Inda degree dinsa yake Alhaji Ashawo,naka degree din Yana Hallare nawa Yana kwakwalwata sabo da kaina ba dai dai yake ba,kabi a hankali bani da kai,Haneef yace nine Ashawo? da mene to nifa ba dai dai kaina yake ba shi yasa ni degree dina na rashin mutunci ne,ba ruwana da wani me gidane kai. Haneef yace me za ayi da jikinki ko dadi babu,ba ni'ima kamas tunda na fara ma ba kwanciya kika yi ba motsin kirki kinyi ne,kuka me dadi ma a danji sexy sound baki iya ba dalla matsa ya ture ta zai wuce,Mero ta tare hanya,zai wuce ta karfi ta rike hannunsa Kam da hannaye biyu tace Kai Abar taka dadi ne da ita? in banda azaba me ta iya tsinanawa,komai baka iya ba,ai baka cika namiji ba tunda kayi releasing a waje kamata yayi kafi karfina ka koma ciki kayi ciki shine kake namiji amma ka kasa kayi half Zina,ai Kai Zinar taka bata inganta ba half kayi,Haneef yaso yayi dariya ya fuske yace a half din kika kwashe satikai kina kuka tunda half ce me yasa kika Dade kina fushi,ai idan ace full complete Zina kayi ni da Kai har abada,yanzu ma da ka ga anmin dole an kawo ni gidanka to Dan half Zina kayi ne,ka daina kuri Kai ba namijin kirki bane. Ai gwarzon namiji shi ke tare budurwa su fafata ta amince da shi ya biya bukata Kai kuwa sai fyade. Koma mene ni naci riba akanki nayi fyade Kuma na aura ki godewa Allah ya wuce sama ya bar mata take away din,farin ciki yake yi akan ta dinga shuru tana kuka gwara su dinga fada kullum yafi Masa. Ledar Mero ta bude Taga kaza, fruits,snacks da abubuwa,ai Mero ta zauna tace dama ita nake jira tun safe Ina gida naki cin abinci,alkawari nayi duk ranar aure na to in za a kaini dama bazan ci komai ba tara yunwata zanyi sai nazo naci kaza ta na koshi,dama yunwa take ji ta zauna taci kaza taci kaza sai da taji kamar zata yi amai sannan ta koma kan fruits ta Sha son ranta sannan ta mike ta shiga kitchen sauran ta juye duk ta adana tare da wanke hannunta ta dawo Palo,Haneef ta samu a Palo a zaune Yana kallo,komawa tayi kitchen ta tattaro ragowar abinda ta taci kaf ta kawo Masa a Leda tace gashi naci nawa ni kanta na gefe,yace ai dama naki ne ba nawa ba ni ba irinsa naci ba,oh dama irinku ne masu cin dadi a waje ku bar iyalinku a gida,tashi yayi yace biyoni muyi Sallah,sai dai muyi a Palo ba Inda zanje,fine ya furta taje tayi Alwala ta sako hijab tazo Palo suka gabatar da Nafila a parlo sannan yayi addua Mikewa yayi tare da furta mata good night ya wuce ba tare da ya jira ma ta amsa ba,haushi taji tace wato yanda suke yi da Ihsan haka zai min bai ma damu da ni ba,duk Ango Yana zumudin Amaryarsa amma ni ko a jikinsa" wato ni ya riga da ya tsotse zagin ba ruwansa,Ina ganin cin fuska a gidan nan,tashi tayi tare da haurawa sama ta shiga bedroom dinta hadadde tayi addua ta kwanta,baccin gajiya da kaca kacar biki ya kwashe ta,Shima haka sai asuba ya tafi masallaci,Mero akwai Sallah akan lokaci bata wuce ta,Sallah tayi da Azkhar,ta duba bata ga Salamatu ba ashe Haneef yace taje gidan sai ya gama amarci zata dawo. bacci ta koma sai wurin 9pm ta tashi tare da shiga kitchen,Shima ya dawo Yana bacci ta hada breakfast ta shirya sannan ta hau gyara gidan ta gama compound namiji ke gyarawa Kuma ya gyara,wanka taje tayi kafin ta fito Haneef ya fito sanye da jallabiya fara a jikinsa,hankalinsa kwance ya zauna a dining kenan ta fito cikin atamfa riga da skert wata golden green tayi kyau kamar ba gobe. Ganin jiya ya shareta yasa Mero yau ta dan sakko baki ta turo tare da furta Ina Kwana?lfy ya amsa a takaice kamar ba shi ba,abincin ta zuba Masa ta hada Masa tea sannan ta zubawa kanta itama,suna ci ba Wanda ya kula wani a ciki,sai satar kallonta yake yanda tayi kyau sosai,sai da ya karya kansa ya fara ciwo Yana Jin zazzabi,Mero tana kallonsa ya dafe Kai Yana yatsina,tace lafiy? Kafin ta karasa ya wuce,tsoro taji tace karfa ciwo ya dawo,ta mike ta bishi bedroom dinsa tace lafiya kuwa? a hankali ya kalle ta yace tunda bakya so na ki barni na mutu mana Ina ruwan ki,wlh duk abinda ya sameni kece,duk lalurar da na hadu da ita kece Sil. Khadija tana Jin yace haka taji tausayinsa ta furta to ai Kaine ka jawo komai muna zaman mu lafiya ka yi min fyade,ki daina cewa nayi miki fyade Khadija kina da shekarun ki,Baki San kaddara ba ke? tunda kince kinyi hakuri kin yafe min ai ya kamata a wuce wannan zancen,Dan Allah ki daina tuna min Ina matukar nadama,kaddara ce ta hauni ba ganganci nayi ba,to wlh sai ka bani million uku ta da na dawo Maka da ita sai ka biyani ai ka riga ka bani,tunda kika kawo min na jefa takardar cikin locker ki duba ki gani,Khadija ta jawo ta ganta a ciki tace to na ajiye abata a nan in ta bace Kaine,Magani ya Sha ya dan kwanta,a hankali ya kalle ta sosai yace kiyi hakuri indai na bata miki rai. Share shi tayi ta dauke ruwan robar Dake ajiye a Saman bed sannan ta haura Saman bed din gefe ta zauna sannan ta furta ka daina bani hakuri,na riga da na hakura,na hakura komai ya wuce,Kinga dama kenan? Ni ba irin Ihsan bace mutuniyar banza mutuniyar wofi Kai wlh da ka sani ma ita kayiwa fyade,ta gama zama ka sake ta Kai da zaka barta inyi kishi da ita,shine ka wani sake ta kawai,dariya yayi yace sai a dawo miki da ita ai,Mero tace tunda ka riga ka sake ta a barta can,hannunta ya rike Yana kallonta kamar zai hadiye ta,masoya an shirya Nan take ya jawota jikinsa ya rungume Yana mata rada a kunne,ture shi tayi tana dariya tace Kai ma fa wlh Dan duniya ne Ina ganinka salihi ashe ashe,light ya kashe Khadija tace haba haba da tsakar rana haka,ya mike ya kulle ko Ina duhu ya mamaye dakin sannan yace sabo da karki ji kunyata in kika Saba ba kashe light,,nifa ban shirya ba gobe sai ki shirya ai please....ya sake hade ta da jikinsa Yana shakar kamshinta ta ko Ina Dake fita lungu da sako,ajiyar zuciya yake saki a hankali Yana shafa gashinta Sakamakon hijab din da ya cire mata,gashin ya Sha gyara,yace a Ina aka gyara miki gashin? Mero tace wata ce a cikin garin Danbatta tayi min,baiyi kyau bane? Muryarsa tana rawa ya furta yayi kyau,Khadija ta lumshe Ido Yana shafa gashinta tace a ranta ashe shafa gashin ma dadi ne ake ji Shima da fa'idarsa,hannu yasa a hankali ya janye zip din rigarta kasa ya bude rigar ya hau sumbata tun daga dokin wuyanta har zuwa bayanta,Khadija a ranta tace yanzu nasan namiji shima Yana da baiwa,a hankali ya janye rigar,duk Mero ta fara mazari itama kamar yanda shi ya hargitse gaba daya,a nutse ya janye rigar tare da balle bra dinta,Albarkatu suka banyana manya a cike dam dam,rudewa ya sake yi ya dawo da ita Samansa a hankali ya cafki bakinta Yana tsotsa Mero Ido ya lumshe tana Maida martani ba tare da ta shirya ba ma,boobs dinta yake wasa da su a cikin nutsuwa,Mero ta gigice tana Jin sweet sai Nishi take yi Shima haka,tace yanzu lokacin fyaden Nan da haka kayi ba sai nayi shuru ba,dariya yayi" tana Samansa Yana Jin ni'ima na fita a jikinta Yana sauka a nasa,Hakan yayi mugun zautar da shi,da dadi ya tambayeta,Mero har da bada amsa tana Jin dadi,a hankali ya dinga koya mata yanda yake so tayi Masa Shima domin Jin dadinsa,abubuwan da take Masa manya ya haukata shi gaba daya Bai San ma a Ina yake ba,Sambatu yake da maganganu marasa kan gado,ya kwantar da ita ya mata sucking sosai Khadija kamar zata mutu ta huta sabo da dadi,sai da taji dadinta sosai sannan a nutse,ya tattara nutsuwarsa sabo da kar ya cutar da ita a hankali ya shige ta,duk da haka dai akwai zafin sai da tayi dan Kara,tace da zafi dan Allah,muryarsa na rawa yana Sambatu ,Khadija tana cewa zafi...ni ayi a gama dan Allah,ba ji yake ba sai da harkokinsa yake bugawa kawai sai da ya gamsu sosai sannan ya hakura,sabo da a haka ma da zai huta ya samu Kari so zaiyi amma baya so yanzu ya sake bata mata rai Khadija ta zama hukuma sai lallashi. Arham yafi sati baiyi komai da Basma ba hakuri kawai yake yi sai dai ya rage zafi indai wannan ne bata hanashi,duk abinda ya nema Basma bata hanawa tsayawa takeyi suyi abinsu,yau da sassafe ya shirya tana bacci ta bude idonta ta ganshi a Jikin mudubi, ci Gaba tayi da kallonsa,sai da ya gama ya juyo ya ganta ta tashi,Murmushi suka sakarwa juna yace kin tashi kenan? tace ba dole ba tunda naji baka kusa ai bacci me dadi ya kare,murmushi yayi yace gida zanje na gaida papa kin San in ana so a same shi sai dai aje da sassafe,to abinci fa baka ci komai ba? Kiyi ke kadai da rana sai naci,in naje gida sai na karya,mikewa tayi tace Allah ban yarda ba,sai dai ka jira,Papa ne zai fita dan Allah ki fahimce ni,to shike nan na yarda sai ka dawo din,takowa yayi gabanta ya mata kiss ya fita ta rako shi har Parlo tana cewa ka dawo da wuri,yace Inshaallah ya shiga motar aronsa ta Basma ya fita. Gidan yaje ya wuce part din Mima Bata Nan tana bangaren Papa,Shaheed ya tambaya Ina Mima wai? tana birnin kauna,dariya suka yi,Arham yace furfura ta baibaye ta me za a samu a birnin kaunar,Shaheed yace uhm to tana can sai dai kaje can,zama yayi ya karya tare da Shaheed yace bacci Basma take yi shi yasa na karya a nan kar ayi min sharri,Shaheed yace ni kaji nace wani Abu? Mima ce ta shugo parlon" Arham yace Oyoyo an dawo daga birnin kauna,me ya kawo ka da sassafe gidan mutane cewar Mima,yace Papa nazo gani ni,tace an kai Ikhy Rafeeq asibiti sai kuje ku ga ya jiki,Arham yace Allah ya raba lafiya,ko banyi niyyar zuwa ba zanje dan naga idon Rafeeq. Papa yaje ya gaisar,Papa ya Kalli Arham yace Ango Kaine ka iya fitowa da safe haka? Arham yace ai sabo da kai na fito kar ace Amarya tasa na manta da ubana,Ina zuwa Kuma naji Mima tana Nan shi yasa banzo ba sai da ta fito,me yasa kaki zuwa zaka min iyayi da ai zuwa kake,to tana Nan wajenka birnin kauna,Ina matar taka? Ina Jin dadi in akace Ina matata,da kuwa sai dai ace ya su Mima,amma yanzu y iyali ana ta ganin mutunci na da girma na,da an San tsiyar da nake shukawa ni da Basma da ba a Kalli girma na ba,ita wlh bata ganin girman nawa ta raina ni,sabo da birnin kauna da ake ta zuwa,Papa yace Kai fa surutun ka yayi yawa Arham, Ina fita mutane salamu Alaykum Malam Arham ya iyali,Papa ya tuntsire da dariya yace tsabar girmanka da ake gani kenan? yace ei,sanda kunwa Ina Gwauro in na wuce ma gulma ta ake yi gashi can Dan gidan sojan cen nan wannan sojan marar fara'a ai dansa ne, ae Jikan Zeenatu,au jikin Zeenatu ne? Cab Yan Duniya ne fa. Papa ya sake Shekewa da dariya yace Maza Mima ta ji kana kiran Zeenatu,Papa yace Arham kai da Spark Ina so kuzo muyi hira aci dariya bakwa rabo da shiririta. Sannan suka tafi asibiti har Mima,Maman Rafeeq tana can da ita aka tafi,Ikhy tayi dauriya tana Jin ciwo amma daurewa take sosai tana cijewa,Likita ta bata wata kwaya ta sa a bakinta,tace ki shiga dakin ki kwanta in kina so Kuma ki zauna a nan ki dinga dan zagawa haihuwa sai anjima,Ikhy tana gefen Rafeeq a zaune tace kyale ni a nan tukun,Rafeeq Yana kallonta in yaga ta yatsine yace Yaya? tashi tayi ta fara zagaye,Maman Rafeeq tace in banda ma tsiya ya za ayi ki sako doguwar riga ki taho haihuwa Kuma doguwar ma wata mannanniya,Arham suna zuwa yaga Ikhy bata saurarar kowa ta kanta take,Mima ta basu kayan data taho da su na sawa,tun Ikhy na zagawa har aka ji ta zauna ta rike mara ta fara barin wasiyya,Arham yace Allah sarki Rafeeq ya kaiki ya baro gashi shi kalau a zaune,Ikhy tace ai macuci ne azzalumi,Mima tace Abu yayi nisa a shigar da ita ciki,Ikhy tace au yanzu Nan da sauran duk bala'in da nake ciki? Maman Rafeeq tace me kika yi Yar nan, shike nan mutuwa tazo na gama yawo,Rafeeq shi ya ma kasa magana addua kawai yake baya kula kowa sai addua Yana zaune bakinsa kawai ke motsawa. Ciki suka shigar da ita,Mima da Maman Rafeeq suna ciki,Arham da Shaheed suka zauna Arham yace su Ikhy ana can ana fafatawa Kai kuwa ba ruwanka kayi mata ciki gaka kana hutawa,Rafeeq bai kulasu ba,sai da aka kwashe kusan hour sannan aka ji kukan jariri namiji,Rafeeq yace Allah yasa ita ce,Arham yace ita ce ma,abinka da private sai da aka gyarata tsaf da jaririn aka canja mata daki sannan Maman Rafeeq ta fito tana washe baki tace nayi jika namiji,Rafeeq ya sauke ajiyar zuciya yace namiji ne? tace ae, yace Alhmdllh babu ni ba yin Siriki da wuri da macece sai saurin girma sai batun aurar da ita shike nan Kuma tawa ta kare to Ina da siriki duk yarintata ai tsufa ya zo kuma Alhmdllh,Arham yayi dariya yace Kai dai masu Albarka ake nema,shiga suka yi ciki yaro kyakyawa katon gaske,Rafeeq ya dauki dansa yace abin da aka shuka a daki a boye an girbe shi yau,Mima tace zaka fara Kai fa a duniya baka da mutunci kaima,Arham yace Mima mene to a ciki muma ba gamu ba kun girbe mu sabo da Allah da ba ayi ba a same mu gamu da yawan tsiya. Chika tana Jin labari tace saura ni Allah yasa Nima na haihu lafiya,Misam yace Ameen Ameen,Naila kuwa,tana ji aka bugowa Spark waya Chika ta haihu namiji Kuma yace wow Allah ya raya Rafeeq ya zama Daddy,Naila ta manna kanta a kunnen Spark wai sai ta ji,ya gama wayar sunce a fadawa Naila yace tana ji ma ya kashe wayar,yace yau dai da babu makaranta banji dadi ba gwara kina makaranta gaba daya,Dan iskanci suma masu makarantar sai su ce yau Monday guda ba lecture,Naila tace wato ka tsane ni yanzu ka gaji Dani kora ta kake yi baka son ganina sabo da ka riga ka gama dani,a baya ai baka so ma na bar kusa da Kai" ba komai,yace sorry Ina so aiki zanyi nasan halinki sai ki hanani da rigima shine fa nufi na,Ba wani wa zaka yiwa wayo,cikin ai Kai kayi min ba wani ba shine zaka ce na dame ka,ta juya ta haura sama da Yar gown dinta iya cinya sama ta tsuke kasa a bude peach ta wuce,Spark yace tab yau akwai daru,tashi yayi ya haura sama Shima,ya same ta a kwance tana waya da Abbanta, tace Abba zancen ka ya tabbata namiji ba Dan goyo bane,ban taba sanin Spark haka yake ba bashi da kirki sai yanzu da na samu ciki,tunda na samu ciki ya juya min baya sabo da ya gama dani,Spark Yana jinta bata San ma ya shugo ba,Abba yace indai ba kishiya zai miki ba ai da sauki kiyi hakuri nima uwarki Kubra hakuri nake da ita,yanzu Nima da na Goyata na sauke ta ,jiya ta karta min rashin mutunci ku dama mata ba hankali ne da ku ba,duk haka kuke Baku da tunani baku da hangen nesa bare ku samu hankali,in kin gaji kiyi yaji ki taho gida Ina da daki spare sai kiyi ta kwana da Beauty kafin mijinta ya dawo,ga Abinci kici ki bar shi,Naila tace na dawo gida Kuma Abba? Ni wlh bazan dawo ba me zanzo na zauna nayi,nifa in ba a gidana nake ba kwana Daya ma a wani wajen kamar a kan kaya nake ji na sannan Kai da zaka min nasiha ka bani shawara sai kace na dawo gida,Abba yace na gaji da yi miki nasiha da fada Naila,ke kanki kin San nasihar nan watarana Yar Inna ce take koya min sai nazo na fada,Naila ta kece da dariya Abba ya tonawa kansa asiri dama nasihar ma ba basirar sa bace,Abba nasihar ma sai an koya Maka? Ai kin San ban iya ba,Mohsin ma yasan gaskiya ba iyawa nayi ba,kin San ta ranar ma da za a kaiki gidan miji kwana nawa nayi Ina biya kafin na iya abinda Yar Inna ta koya min? Shine ai kika ga na zage Ina ta fama uwarki ce ta koya min ba yin kaina bane,ai karshen abinda zan iya nace Allah ya tsare a kula shike nan,Naila dariya take kawai,Naila tace Abba baza ka Kara da Yar Idea Dinka ba? Idea me Ina na ganta sai wacce ba a rasa ba,da fa ma ace ba sunana Hashimu Dolo ba to da sai a samu canji amma indai nine to sai dai kuyi hakuri Abbanku bazai iya abin duniya ba,ku godewa Allah da nake iya sana'a ko da akan katifa ne. Abba yace ban fada miki ba mijinki ya siyo min sabuwar mota me tsadar gaske Baki ganta ba,ga Mohsin tun kafin ya dawo ana ta canja mana gida za muyi gate da wajen ajiye mota,gidan Sale makwafcinmu ya siye shi ya hade da namu aka rushe za ayi katon filin da gate gaba daya gidan za a sake,Naila tace mashaallah an gode to driver zaka dauka? Ina fa na barwa Yar Inna ita halak Malak ta dinga tuka ni duk Inda zanje ta kaini tunda ni dama ba wani fita nake ba,Yar Inna yanzu ta fara koya sai Murza kan mota take yi nace iyyeee uwar Naila taci gaba,Naila tayi dariya tace Abba ko driver baza a dauka ba? Yar Inna ta Isa rabu da ita Jaruma ce,shike nan to a gaishe ta yace zata ji ,Dan Allah ki zauna lafiya da mijinki,ke irin laulayin uwarku kika gado wlh hayyata,cikinku hayyata, ku hana miji sukuni,ki dinga hakuri,wa zaki samu irin mijinki a yanzu,Naila tace ai shine yake jawowa,Spark ya harde hannaye a kirji kawai Yana jinta,tace ai shine ba Dan goyo ba Abba,kune kuke ganin kirkinsa ni yake kunsawa takaici ku ya faranta muku sabo da Kuga kirkinsa,haka yake min abubuwa iri iri ta karkashin kasa shuru nake kawai Abba,Hashimu yace in zaki kwana bazan yarda ba karya kike in da gaske ne ai nace kuyi yaji ki taho mana,a'a Abba ni ka daina cewa na taho gida ai ta wani bangaren Yana da kirki,Kuma ma laifin kadan ne ai,gaskiya ba laifi,Abba yace ayi sai nazo na taso keyar Yata ta dawo gida Ina amfanin zama cikin hakuri da takura,ba sai kazo ba Abba ai Yana kamantawa da kirkinsa,Kuma fa Yana so na kawai dai watarana sai naga Yana min gani gani,zanyi zamana,Abba yace bari na kira shi na kare Masa tanadi,Naila ta furta a'a ba ruwanka Abba ni zan iya da kaina, Abba dariya yayi tun a sannan yasan tsiyar Naila ce karya take ba abinda aka mata dama gwadata ta doayi,sallama ya mata ya kashe wayar,tana Juyowa taga Spark tsorata tayi ta dafe kirji wayyo Allah dan cikina,wlh ka bani tsoro,sai ka dinga min labe kana Jin sirrina haka ake yi a duniya,yace Maza kiyi ta Kai karata iyaye dai tun basa yarda watarana zasu yarda,zaki jawo su tsaneni a banza,suce Ina miki wani Abu,to baka yi din ne? Naga rannan da nace ka siya min ankon wata cewa kayi baza ka siya ba direct ka fada min,na hakura ban ce komai ba banyi zuciya ba na kawo Maka wani agogo nace ka siya min kace to kawai ka Maida ni banza ko zancen ma baka sake yi ba,nayi shuru Nima rannan har gida Matar Yaya Khalil ta kawo wani material da kana Nan kaya tace ka siya kin siya kayi,da Sanda Ina waje ne nayi Imani jikinka na rawa zaka siya,sabo da yanzu nazo na gama yawo kayi min ciki,shine ko yaushe ka kora ni makaranta sabo da baka son ganina nima na daina zuwa makarantar bazan je ba,na fasa karatun tunda badan Allah ka sani ba sabo da ka tsaneni baka son ganina ka kaini school,kullum ban isa inyi fashi ba ka dinga masifa kenan kace Ina Maka asarar kudi haka ko bana Jin dadi sai ka kaini school ta dole to bazan je ba na daina makarantar in zaka Jani ta karfi ka Jani ka kaini,ka isheni ni na gaji duk nabi na tsane ka ma,wani kyanka wani kudinka, wani surarka,wani hallarenka,wani iya Uhum Uhum Dinka wani iya sarrafa uhm uhm Dinka,wani komai naka baya min ya daina min,yawwa ka daina ganin wani kana ja baka ja a wajena baka tafiya aradu,in sanda Ina kauye ne ka min wannan tuni sandata bata sha jininka ba ban fasa Maka Kai da Sanda ta ba,wul wul Ina wulwulata sai dai kaji gaf a goshinka,karka kaini bango ka bari na dawo Tantiriyata a gidan nan wlh baza ta maka kyau ba....tana gama masifarta tace an dai gode Maka ka siyawa Abba Mota again,tanan wajen dai anyi basira Allah ya Kara budi mun gode sosai da sosai. Spark Yana kishingide Yana kallonta har ta gama yace Uhmmmm....kawai,tace da anyi magana an Fadi gaskiya kace Uhmmm,Uhmmm fa baza ta kaika ko Ina ba,Anbi a damu mutum,da ace ma akwai Inda zan tafi nayi sati biyu na huta ba shike nan ba,fitar ma da na tashi fita nace zanje waje kaza,to Baki da aiki ke sai unguwa Yan..Yan ..yi..yi..ya...chaccha baza kije ba,ke kullum yawo,Dan bado abin alfahari na ba dama na hana nace bazan bayar ba bana so sai an min fyade,kullum fyade ake min a gidan miji,Spark Yana jinta Yana dariya a ransa,kwanaki ma ni me miji wai ni irin zan samu Lada na zauna na sharara Maka wanki nayi guga,yini nayi Ina aiki a kayanka irin zan samu Lada, dake kai ba a ma gwaninta wai kazo ka gani sun fita kuwa ai da kin raba biyu,ke ba iya wanki kika yi ba karki Bata min kaya, maimakon kace wow Baby my life,My Heart Allah ya miki Albarka Allah ya saki a Aljanna shuru kake ji,nace ko Albarka baza ka sa min ba? Wai Allah ya saka miki a baka kiji dadin tauna,na tauna me to shinkafa? a lokacin kyaleka nayi zazzabi nake shi yasa banbi ta kanka ba,,Allah ubangiji ya kawo ranar da masu wanki da guga zasu yi yajin aiki ko Kuma wata matsala ta samu,ka rasa me Maka wanki gashi ka sake kayanka gaba daya tas baka da na sawa muga waye zai wanke Maka ko Singlet,Kuma wlh ko basu yi yajin aiki ba Ina Nan sai na kulla Maka takaici akan wanki zaka ga tsiya,kayan zan samu duk na jika su na barsu a haka,sai ka damu da wanki Ina nan da Kai. Spark yayi dariya kamar ba gobe,Masifar Naila laifi tun Wanda ya wuce baya sai an tono shi an dawo da shi sabo,yace to duk naji kiyi hakuri,ba wani nan sanda Ina budurwa da nazo gidan Nan har Indomie da Salat na Maka ka cinye abinka tas harda ya bawa Ashe Ashe ladabin duk na bado ne,Ashe kace shegiya gama yinki sai nan gaba zaki ga Spark,ni Kuma na dage duk duniya my Spark Ina kuka akan Spark ya rike Wahida Dan Allah jeka yanzu ka rungume ta wlh lafiya zan kwana,ba wani in ba Kai sai rijiya,wani sai da Kai zan rayu gwara a bani shinkafa Yar Hausa,ko tsakin shinkafa,Spark ya dinga dariya kamar me,daga yace me yasa malamai suka ce yau ba lecture,yace naji to I'm sorry shirya mu tafi ganin jariri,Naila tace a'a kaje na taho Ina zan bika na takura maka baka son ganina ai ba na zauna kusa da Kai ba,sai ka dawo,ya buga ya buga tace baza ta bishi ba ita kadai zata je,sai da ya tafi ta shirya ta shiga motarta taje asibitin da abinci lafiyayye,Mima tace Spark ba daga gida kake bane na ganka Kai kadai Ina Naila? zata zo yanzu aiki take yi bata karasa ba,suna haka sai ga Naila ta shugo,suka gaisa ta dauki jariri tana yiwa me jego sannu,Rafeeq ya fita lokacin,Naila ko kallon Spark bata yi,kamar bata sanshi ba tunda yace me yasa aka ce yau ba lecture to baya son Ganinta ita,ko dadewa Bata yi ba tace zata tafi,Mima tace tun yanzu daga zuwa,tace aiki zanyi ne zan dawo zuwa yamma,lokacin ma an sallame mu sai dai kije gidansu tace to ta musu sallama ta tafi,Mima ta Kalli Spark tace ko dai laifi kayiwa Naila ne naga kamar ranta a bace? Spark yace tunda cikin nan ya samu haka take yi fa,a'a naga bata ko kulaka a yanayin da kowa ya sanku yasan yau da matsala,Spark yace fushi tayi fa,cewa nayi me yasa ma yau Monday guda za ace ba lecture ai gwara ta tafi school shike nan fa,Mima tace ko nice wlh sai naji haushi tsakani da Allah baka kyauta ba,Dan me zaka ce haka,ya nuna ka gaji da ita a gidan,Spark yace wlh ba haka nake nufi ba ni nufina sabo da fitinarta na tsokane ta Ashe haushi abin ya bata ni tsokanarta nayi ,kawai,to baka kyauta ba gaskiya,ka takura mata da karatu a farko Kuma ka nuna baka so sai yanzu ka dameta Kuma kasan tana da lalura,yanzu Mima waye baya kuskure a Dan Adam shike nan mutum bazai laifi ba ai dukkanmu Yan Adam ne sai ana uzuri,to dai ka gyara,ciki ne ya sata koma mene kayi hakuri da ita a haka har ta haihu,nufinki bana hakuri kenan? yaushe nake mata laifi duk abinda zata yi bana kulata fa shine yau kawai Dan ni nayi sai ace,ai ku ba a Baku shawara ku dauka Gani kuke kunfi kowa sani,ai Naila ce gaka nan gata ai ba kyaleka zata yi ba cewar Mima,tun yaushe ta rama fadan,ta rama abinta,ta kusa 1hr tana surutu Kuma bance komai ba hakuri ma na Bata,nace tazo mu tafi tace baza taje dani ba,Mima tace ko nice bazan je da Kai ba,Spark yace ke haka kikewa papa wlh ba haka kike ba akwai wacce Papa ma yake juyawa irinki,dukan Spark tayi tace ubanka" Dan Ubanka sa'arka ce ni,dariya yayi yace wlh juyaki dai ake yi,mu Kuma gashi ana juya miki yara. Bikin Rahma da Nabeela ake yi mata sai sintiri suke a gidan Jauro,Abba da Jauro sune waliyyan Amare,sun Sha kyau,Abba Yana jiran Jauro a kofar gida zasu koma gidan Maman Annoor su huta a can Jauro ya fito yace Kai mata dai sai dai ka gaji ka barsu baza su kare ba kullum kero su akeyi,wata Yar budurwa ce ta wuce Abba yace Jauro ga wata nan,Jauro yace wannan baza tayi quality ba irinsu ne masu kwanciya ba shara bare wanke wanke,kawar Rahma ce ka ganta Yar talakawa ce futuk,Abba yace ba ruwana da gulma a kirata a fada mata ko ayi a gabanta,wata bazawara tana wucewa Jauro yace kaga dai dai mu,Allah ya Kara lafiyar kwalliya,Abba yace shiga mota mu tafi karka sa mu kwashi zunubi,Hidaya ce tazo itama Abba yace ga 'yata Nan Yar tsila anyi kiba ya fada yanda Hidaya zata ji,wajen su Abba tazo ta gaishe su,Abba yace su Hidaya daga gidan Siriki sai gidan miji unguwar mu ma an manta,dariya tayi tace Abba rannan fa naje baka nan,yace uhm ya zanyi tunda an raba mu kiri kiri,Ko Allah Sanya Alkhairin mota baki mana ba,Hidaya tace ai zanzo na ganta Abba,yace Allah ya kawo ki idan Manniru Dan Jauro ya barki yanzu ya rabani da 'yata sai abinda yace,Abba Kai fa ka dage sai na aure shi,ai ban San haka zai min ba ya raba 'ya da iyayenta,in samu jika guda duk ku kasa taya Yar Inna suyar nama sai ma'aikata ta samo mutum biyu suka yi aka biya su,Hidaya tayi dariya tace Abba ka gaida da Umma,wato ke Nan kinzo gidan siriki Jauro jeki Allah ya taimaka,Hidaya ta tafi tana dariyar Abba,mota suka shiga suka bar gidan. Anyi biki lafiya an Kai Amare . Arham sai 2pm bayan yayi Sallah ya koma gidansa ya samu Basma a kitchen fitowa tayi tace ka dade Allah tana shagwaba...rungumeta yayi tare da furta matar Rafeeq ce ta haihu naje,kukan shagwaba ta fara Masa tace nifa bazan je ba? Zan kaiki mana amma yanzu na gaji,yanzu yunwa nake ji har kala biyu,wacce? Ta abinci da taki yunwar,Basma kamar zata yi kuka tace ban fa warke ba Allah,Arham ganin bata hanashi komai yace please Gidan ya kalla ko Ina ta gyara shi sai kamshi da kyalli gata Basma ta Sha kana nan kaya,ta zuba kyau gaba daya sai Arham ya rude,ya zauna a dining tayi serving dinsa,Yana cin abincin girkin ya Masa dadi,amma hankalinsa na kanta gaba daya,spoon din ta karba tana bashi a baki,ya jawota tare da Maida ta Saman cinyarsa yace washhhhh.....na koshi sai kin bani Bado sai na dawo naci gaba da ci,ya Sha lemon da ta hada ya dauketa,ta fashe da kuka tana tunanin wahalar da ta Sha a farko. AsmaBaffa [3/7, 10:35 PM] AsmaBaffa: 🏫TANTIRIYA🏫 A GIDAN YARI BOOK 3 ~TAIMAKO~ 76-80 Official By AsmaBaffa SADAUKARWA NE GA AIDA MAMAN TASNIM PAGE NAKI NE Humairer Dan kukan da Basma take yi ko a jikin Arham yace yau bazan lallashe ki ba sabo da babu tausayi yau a jiki na,yanzu baza ka tausaya min ba,yace a'a akan me kina lafiyarki kinsha zama cikin ruwan zafi ma karewar azaba bare ni da Hallare ce kawai,ruwa da zafinsa rau rau ki watsa gishiri ki shige kiyi dabas ciki sai kiyi hour a ciki,har abubuwa naga ana kawowa kina tafasawa su ganyen magariya ce ki zauna daram a ciki duk zafin Nan bakya ji sai Hallare me Sanyi da taushi, ko tausayina bakya ji,Basma tace to muyi romancing yanda kake yi kullum,Ina ma'auraci wannan bazai haifar min da me Ido ba,bazai taba daukana ba,bayan haka ma zance nazo gidanku da zaki ce sai tabesting,da aure na da komai amma Wanda ke zuwa zance ma ya fini releasing bazan iya ba. Bedroom ya kaita tare da kwantar da ita yace ke mene na kuka ni da zamu tafi Honey moon ni da Spark na je can na samu international water a jikinki, International ni'ima,Basma tace ni ban gane ba,to a Nan kina tunanin an rufe kofa ko ba a rufe ba,kina tunanin zaki girki,zaki shara zaki gyara gida,ko waye da waye a can kuwa kin San ba komai muka je yi ba shakatawa kawai zamu yi sai dai mu siyi abinci muna hotel muci me kyau mu Sha me kyau me zaki tara in ba International ni'ima ba,dariya Basma tayi tace hmm,yace ba ni na fada ba wlh Spark naji Yana fada wai zai Kai Naila yawon duniya ya ja International water,ai shine malamina,duk wata magana in kika ji Ina fada a wajen Spark na koyo,idan kika ji Kalma me nauyi kamar zata tarwatsa dodon kunne to Rafeeq ne,a aikace Kuma in kika ga Ina aikatawa to Misam ne shine ya koya min,ba ruwan su kaima kwallo guda ne ba wani,anyi haihuwa zamuje ki bari Muji dadinmu sai mu tafi,kar na tafi na dinga kallon Yan barka matan mutane sun zo barka,Basma tace tab ai kuwa sai dai kaji na makeka akan me wlh sai na shake ka a gaban mutane,dariya yayi tace Allah yasa yau ma kayi min kyauta wlh sai ka bani abina,Arham yace bazan sake bama amma wlh da ni me kudi ne irin Spark ai da yanzu na miki kyautar gidan nan na Gina sabo mun koma. Yanzu dai sunshine a baje Sunan wata waka,jikinta ta kankame tana shagwaba duk ta Kara tunzira shi da shagwaba,daga fara kiss ta karbe,hannayenta tasa ta wuyansa ta sarkafo,Arham yace Basma ba rowa haka nake so mace bata rowar kayan alatu,Basma taji zuga tace ai dan ma da zafi ne Ina fara Jin dadi wlh ko yaushe marhabun lale da kai my life,Arham harda shagwaba,Yana mata wayo harda kwanciya wai a shayar dani in Maza in shiga paradise,Basma tace duk sanda na haihu zaka yi kukan rashi,yace wa? Nufinki na barwa jariri nonon? ae mana,yace wlh bai Isa ba ko waye ubansa a kasar nan,to ai Kaine uban nasa" to kuwa ni ubansa ban isa ba dole ne Ina nan,yaro yazo sama takai ya rabaka da komai,Allah sarki Rafeeq ai dole ma naje gidan me jego naga idon Rafeeq ba Kwalbewa,Basma tana magana tana shafe Dan mijinta suna ta surutunsu kafin Abu yayi nisa tana surutu taji Arham shi Kam ya zauce abinda take fada daban amsar da yake bata daban,biye Masa tayi Yana sarrafa ta itama haka,ya tsotsi nan ya Murza can a hankali cikin nutsuwa kamar bazai yi komai ba yanda yake lugwigwice Basma sai da ta fita a hayyacinta hankalinta ya gushe, harda hawayen dadi Yana licking dinta,tana kukan sweet,ya matsu ya shiga amma ya daure sabo da taji dadi itama,Basma cewa take Ina sonka mijina.....wayyoooo....Arham kuwa sai Yan iskan kalamai yake,a hankali ya samu a nutse ya fara kutsawa cikin Basma,Jikinsa na karkarwa Yana shidewa Basma ta fara ture shi,ko ta kanta baibi ba,Dan ya tausaya mata harda cewa dinki na ya farke,Yana Sambatu yace in na gama na dinke miki sai kace wani skirt ya yage,Arham ya dinga buga harka Yana Sambatu iri iri,ko me kike so na baki, Basma lokacin tana Dan kukanta tana jinsa,ko mene ne indai nawa ne na bar miki,Basma tana kuka taji ya fada karo na uku ko mene na baki,komai nawa na bar miki,Basma tace to..to zan dinga dauka a hankali Ina karba. Sai da ya gama rakashewa ya gama Jin dadinsa ya huta sannan yace yau ai ba wahala sosai ko? tace Kai da zafi yau ma amma dai da sauki duk da haka sai dai tafiyata da kyar zan iya kawai hakuri nayi kar kace na fiye raki haka Naila tace na dinga daurewa kafin na Saba,Arham ya kankameta yace Allah ya mata albarka tana Dan gyara min matata, tace yawwa Ina son agogon Nan naka ya min kyau mata ma naga suna sawa yaran masu kudi,Arham ya zaro ido,Basma tace Kaine kace komai naka ka bar min wlh Ni dama na Dade Ina son agogon Nan naka,Arham yace Papa ne ya siyo min kin San tsadarsa kuwa wannan? Ina ruwana ai Kai kace komai naka ka bar min,waccen karon ka min kyauta Naila ta bani hakuri na hakura wannan karon bazan yarda ba,Arham yace to Kya dinga bani aro kin san kayanki kayana nane ko? Basma tace na gaji da ara maka ayi min kyauta kullum kace aro,daukanta yayi Yana cewa bakina nane da yaji bado ba saiti na rasa dalili Allah yasa mu samu Naila a gidan me jego. Wanka yayi mata tare da gasa ta sosai tana raki haka suka yi wanka tare da tsarkake jikinsu,suna fitowa ya gyara bed din da dakin suka shirya,ya hade cikin 3qutr da riga me gajeren hannu wasu blue sun Sha kyau,Basma ta fito cikin Material gown me Fadi ta Yan gayun Abuja ta dan yafa mayafinta kace Yar budurwa ,komai shi ya mata,tafiyar ma da kyar take yi,tace yanzu haka zan shiga mutane? Arham yace ai ba zina muka yi ba muje baza ma su gane ba. Abincin su ta gani kamar za ayi asarar sa zasu bar gidan,yace baza kici abincin ba? tace wlh ni tuwo nake so naci yanzu,Arham yace tab muje a bawa me gadi wannan in muka je nasan maybe a samu tuwon a can. Suna bawa me gadi suka shiga mota abinsu,a hanya ya kira Mima yace me jegon a Ina take yanzu? Mima tace tana gidan Maman Rafeeq tayi Masa dole tace wlh baza su zauna su kadai basu San ya ake Reno ba,Kai kaga fushi wajen Rafeeq tab ai badan yaron nan jariri ba bazai sake zuwa gidan Mama ba,shi sai dole matarsa ta koma gida,sai da na hadashi da Papa ya hakura. Arham yace to kune ai da takura yanzu an daina wannan abin Kuna yawa gaskiya,Mima ta kashe wayarta kawai,a hanya suka yi siyayyar Fruits da yawa suka tafi da shi. Spark kuwa Yana komawa gida yasan fada zasu yi da Naila ya bata haushi,abin mamaki Yana shiga ya ganta a kitchen tana girki da fara'a da komai kamar me aljanu haka take yi,tana Juyowa ta ganshi tace sannu da zuwa ta rike hannunsa,tace tuwo nake yi zan kaiwa me jego zo ka dandana miyar nan kaji,hannu ya mika Yana murmushi yace dazu kika gama masifa fa har kin huce? Naila tace Allah sarki yi hakuri Dan Allah ka yafe min kaji,Kai ba fa kamar ka a wajena,Spark yayi dariya yace Allah? tace hmm wasa kake da kaunar da nake maka,Nifa yanzu a bani shugaban kasa ace na barka to suje da shugaban kasar su,Spark harda Jin dadi Yana kallon Naila Yana shafa gemunsa me kyau. Naila tace ba wani shege a kasar nan "Allah",dariya ta kama Spark musamman yanda ta wani daga gira ta fada da sigar yan zara,yau sai ka raba dare kana wasa Hallarenka a Bado, a sake wasa ta tayi kaifi,kasan yanda ake wasa wuka idan za ayi yanka? yau shi zaka yiwa hallarenka sai dai aji kuyas kuyas,Spark ya sheke da dariya,tace to waye yake da irinka in ba ni ba? Wata soyayyar ma sai mun hadu a Aljanna,idan ba za a ga kauna ta musamman,fuska ta kwabe tace sai dai Ina da kishiyoyi,Spark yace ai kece Shugaba sai abinda kika ce,Spark harda cewa tab zasu ga banbanci Ina wajenki kullum,dariya suka yi,yace bari naje nayi wanka na huta a gama tuwo naci,amma zaka kaini gidan Me jego anjima da yamma ko? Yace as you wish. Naila tace Baby a rungume ni ya rungume ta suna dariya tace to ka shafawa danka Kai,Spark ya shafa ciki yace Salam Baby dan Baby kana zuwa duniya akwai meeting sai anyi family meeting a kanka,to je kayi wanka cewar Naila,kiss ya mata ya wuce,yace Allah yasa ya dore wannan nishadin. Sai da yayi wanka ya kwanta ya Sha baccin ranarsa sai 4pm kafin ya tashi Naila ta shugo tace ka tashi haka har nayi sallah,ni ka min ciki ka barni na zama jagwal Kai kana ta baccinka lafiya,indai haka ne kowa ya daina baccin rana a gidan nan. Spark ya tashi dariya yayi ganin ta a turbine kamar ba ita ba,yace dazu dazu fa kika bani hakuri kika ce na yafe miki, me na Maka da zance ka yafe min? Ni baka ga laifin da kayi min ba,ganinsa tayi ya mike ba riga daga shi sai boxers baki ta washe tace na yafe Maka,na yafe muje na Maka wankan tana kallon bayansa lukwi lukwi da shi,Spark tunda yaga haka yasan cizo take so,idan yace baya so fushi Kuma, yace muje,ta mike tana shafa bayansa tace Allah ya Maka baiwa, Spark yace Alhmdllh,toilet ta bishi suka shiga tana wayo tace inyeeee Spark din ba jiki duk kyau dumi dumi da kai,Yana boye dariyarsa yace Dan Allah cije ni ki huta ki daina damuna kamar mayya,da haka kawai yace mata kamar mayya cewa take ya mata kazafin Maita sai ta saka kuka,amma yanzu harda cewa ni ba ruwana wanka kawai zan Maka,mu Kwalbe a nan kaji please tana shagwaba,yasan manufarta Yana cikin Kwalbewa zata cije shi shine burinta,wayo ya mata yace to ai kuwa kin kyauta min ya jawota jikinsa suka fara sarrafa juna,sai da ya shigeta hannu yasa a dai dai wajen bakin ya toshe yace karki min ihu da yawa nasan halinki,ni ka sakar min bakina..zanyi ihun dadina...ta fara kokawa da shi tana Fisgewa,gashi tana enjoying sosai haka ta hakura suka kwalbe iya Kwalbewa sun Dade suna abu,wanka suka yi suka tsarkake jikinsu,Spark yana wani jinsa zam zam ya manta da batun cizo ta zagayo ta bayansa tare da cizonsa a baya ta arce da gudu tana dariya,sabo da sauri ma ko zafi bai jiba kadan ta cije shi,Yana fitowa tace fyade yayi mata bayan dadin da taji abinta ta manta. Suna shiryawa tace ni yau Hijab zan saka har kasa Spark yace ai Yana miki kyau,tace to Allah kwalbewar yau tafi ta kullum dadi idan mun dawo a Kara,yace ai ke kullum dadinki na daban ne,sai naji kullum kamar sabuwar Amarya na aura daban, kullum dandanon na daban ne,Naila tace tunda aka yayeni nake Shan madarar shanu me zafi, Spark yace ai kuwa gashi Ina ta Shan tawa nima ta jikinki,so nake fa mu bar kasar Nan Kwanan Nan in samu International water in baki International milk,dariya tayi ta Dake shi a kirji tace Allah da sa'ana nane kai yanzu sai nace shege mutumina amma mijina ne kafi karfin haka,sai dai Kai a zageka da bado ko?,Spark yayi dariya kamar ba gobe yace ai kin zage ni ma,ambola zan na Maka da bado yanzu in ka bani haushi,Spark yace kice akwai kallo,ni Ina so wlh a dinga min kullum. Spark jallabiya ya Sanya suka tafi da girkin Naila kala biyu. Suna zuwa a can suka iske Misam da Chika da tsohon cikinta,gidan Maman Rafeeq daki guda aka ware,me jego da Mijinta suna zaune ga Arham da Amarya an kame a gefe,Spark Yana kallon Arham ya tuntsire da dariya,shi dariya yake bashi a dole me mata yayi aure ya zama babba,Naila ta haye Saman gado tace to mufa yanzu sai an mana uzuri Kuma,Ikhy tana zaune ta Sha kyau cikin Abaya ta saka hula peach kalar Abayar,Naila tace ga tuwo me jego,Rafeeq yace Allah miki Albarka shi take nema yanzu ko? ya leka fuskar Ikhy,Arham yace mu gani da yawa? Ya bude flask din ya Gani da yawa ya Kalli Basma yace ya miki? tace mu Gani miyar mece? ya bude Taga kubewa Danya tace an sa man shanu sabo da ni nafi so da man shanu,Kiyi manage haka ya dauki plate da spoon ya zuba mata tace yayi haka ma,Rafeeq ganin kanin su ne da matarsa kar su disga shi suka yi shuru, ya ishe ki? Rafeeq ya tambaya, tace ya isa haka,Naila tace Arham Ku na dafawa na me jego ne ai ka bari ta fara ci kawai Kai matarka ka sani. Arham yace sai muyi zuciya mu fasa ci Dan kin samu ma za aci,faccalanci zaku nunawa matata wato ku kun hade Kai Yan gidan yari akan wani tuwo,to tayi girkinta sabo da zamu zo nace kar tayi tuwon za a samu a nan,kayan Rafeeq ko Spark kayana nane,Naila tace na shiga uku au haka ka fassara min magana,kana jinsa dai ko to ya Kalli Spark,Misam yace to ku yanzu mene haka akan tuwo,kema da ya eba sai ki kyale shi mene a tuwo baza ta iya cinyewa ba,Chika tace to daga ta danyi magana sai yace faccalanci muke idan yarinyar ta dauka fa a ranta,Rafeeq yace ku bar maganar dai,Arham taci tuwonta Ikhy Rafeeq ma ga tuwonta,Ikhy tace ni yayi min ma yawa,Dan uwarki haka zaki fada min in zage in miki kice ya miki yawa? Cewar Naila dariya Ikhy tayi tace sorry madam. Spark kuwa baice kala ba,ko kulasu baiyi ba sabo da idan yayi magana zata ce ya tarewa Dan uwansa ko Arham yace ya tarewa Naila shi yasa bai ma yi magana ba. Sai da Arham ya ajiye tuwon yace ga abinki nan Me jego taci lafiya,shi kanshi Arham ba a fada da shi bai ma da saurin fada kawai wannan lokacin ne shedan ya shiga tsakani,Spark ya Harare shi yace in zata ci taci abinta bana son iskanci,Kai baza ayi Maka magana ba,dauka kici tuwo,Basma ta dauka tace dama ni Ina so wai bazan ci ba ai ba Dani aka yi fadan ba ta dauki tuwonta. Spark ya Kalli Naila yace daga yau me Kuma bana so Dan kinyi Abu wani zaici kice ba shi kika yiwa ba,koma waye ba sai Dan uwana ba in zai cinye du ya cinye,Naila kamar jira take sai Kuma ta rufe fuska da hannaye,shi Arham ma dariya abin ya bashi,yace kiyi hakuri Aunty Nailan mu,munafuki sai da ka hadani fada da mijina sannan kaji dadi sai yanzu zaka bani hakuri,sabo da kayi aure,da kullum kana gidana ba abinda bana yi Maka shine yanzu akan tuwo na danyi magana shine zaka nuna ma kamar ban taba kyautata Maka ba. Arham yace to ni da kitchen ma nake shiga kice na ebi abinda nake so har kudi kike bani kiyi hakuri ban San ma me yasa naji haushi ba wlh,Misam yace ai yanzu malamar kuka ce Naila idan Hallare kike so akwai waje ga Kuma Oga kusa,Rafeeq tace wayyo ni maraya ta kare min,Dan Allah bakwa Jin tausayi na? Uban wa zai tausaya Maka? Inji Misam,Ikhy tana ta cin tuwonta,Rafeeq yace Ina cikin wani hali na shiga tangal tangal Kuma,Spark kayi hakuri zaka yi asara da yawa a Office don baza kaga dai dai ba babu harka ba aiki asara kawai kamfanin zai dinga yi,Spark yana can Nailansa na kuka hankalinsa ya tashi ya dauki waya Yana mata text na bada hakuri ko kula su Rafeeq baiyi ba,Yana tura sako Naila tana goge hawaye tana shesheka ta duba wayarta taga ya rubuta Dan Allah kiyi hakuri kece da gaskiya ba Arham,Arham ya nuna Rashi tarbiyya a Nan,ya nuna gidansu ba home training,haba my Baby,Yar Abbanta Sweety na Naila Hashim Text ce ta biyu ta sake shugowa ta duba yace Hawayenki tamkar ruwan zafi ne ke zuba a zuciya ta Dan Allah ki daina kukan nan my Heart,haba Ruhina Auntyn Hidaya da Zarah. Naila aka gani tana duba waya tana faman zuba murmushi,kwanciya tayi a Saman bed din,ta juya tana facing din Spark,text ta tura Masa kazo ka share min hawayen to,Spark yaji kunya yanzu ya gama yi mata fada da muzurai sannan aga yazo Yana share mata hawaye ya nuna shike nan ba jajirtacce bane,Kallonsa tayi ta sake sabon kuka,ba shiri ya matso yace Arham Miko min tissue,suka kwashe Masa da dariya,Misam yace Dan iska kace baka ji Kai a dolo ka taba shiga Soja,na rantse da Allah nasan karya yake wannan fadan ai bazai iya ba,Spark yayi dariya yace Yan hassada,ya goge mata hawayen tas,Chika da Ikhy suna kallo suka ce ja zarenki Tantiriya,kina harka,Naila Bata kula su ba tace kayi hakuri idan na Maka laifi kaji,Misam yace ba sai kince ba ma ya hakura ai baya fushi dake,Arham yace tsumin kauye ce ai sai da aka hado ta tsaf aka kawota gidan,Rafeeq yace a dinga tausaya min Dan Allah ga Ikhy ta gashi ba damar Uhm uhm. Spark ko kunya sai Lilita Naila yake. Basma tace Aunty Naila Kinga dai rannan da kyar kika bani hakuri na hakura akan kyautar da mijina yayi min,to yanzu kinji an Kuma wata wai bazai bani ba Allah wannan karon bazan yarda ba,Rafeeq yace wacce kyauta ce? Arham da sauri ya toshe bakin Basma yace ba a fada,wlh dama nace na gaji da rufa maka asiri,Malama Ikhy tace dole na ganki Basma na jawo Aya na jawo hadisi,Arham yace yawwa Malama a taimakeni,sai Kuna janta a jiki,yarinya ce,Chika tace ke ba wani kyauta da za a baki ke baki San Kwalbewa bace suka sa Basma a gaba,wannan tace wannan tace. Mima ce ta shugo da Maman Rafeeq da mata Yan barka,Mima tace ku kadai Kun cika daki,Shaheed ne ya shugo da junior tare da Mufee Amarya da Haly,Mima tace dalla ku tashi ku fita ku bawa mata waje,Kai Rafeeq kuyi waje. Arham tashi maza ku koma daya palon,Rafeeq yace jikokin Zeenatu ne basa jin magana gado muka yi,Mima tace kasan Allah....tashi suka yi,ta Kalli Spark Yana gyarawa Naila hijab ta make hannunsa tace tashi idan ma da matan zaku tafi kuje,Arham yace to ku bamu danmu mu tafi dashi,Maman Rafeeq ce ta hayayyako Masa da masifa wannan yaron ni Sam ya fitar min Kai tunda rashin kunyarsa ta Kai karshe,Zeenatu wasa ce? Jikan Zeenatu ne fa cewar Misam,suna fita aka bar su Mima mata suna ta shugowa barka. Tunda aka yi haihuwar kullum su Naila suna hanya har aka yi suna yaro yaci Suna Abdallah,Yan uwan Ikhy da matan Yahuza sunzo,Haidar ma yazo da gift,Ikhy ta Sha kyauta. Sati biyu da haihuwar Ikhy, Chika cikin dare ta kasa kwanciya,ta kasa zaune ta ka kasa tsaye,tun tana daurewa tace Misam ka tashi mu tafi asibiti wlh bayana Marata,bayana zai tsage, wayyoooo Babana,kafin ya shirya su tafi ya dakko tarkacen haihuwar da ta hada har ta fara ihun kuka,Chika da bata da raki bata da saurin kuka amma ta fara sheka kuka ,gidansu ya kira matar Marikinsa ya kira Mima ya fada mata,suka tafi asibiti a can su Mima suka same su,a daren ana zuwa Chika ta haihu Bata yi doguwar nakuda ba sai kukan tsiya,ta haifi yarta mace santaleliyar gaske. Sai washe gari da safe aka sallami Chika. Beauty kuwa Mohsin Bai fada mata zai dawo ba amma ya fadawa Abba,yace kar ya fada mata,amma Abba ya shugo gidan sai da yaga Beauty ya dauki jariri yace an fada min wata magana ance kar na fada inji mijinki,Kamar na fada kamar kar na fada,Kubra tace ka fadi me? Dan Allah kazo dama Ina son magana da Kai duk wai Dan kar ya fada ta janye shi,da kyar aka samu Mohsin ya dawo Abba Bai fada ba sai Jin Sallamarsa aka yi da yamma Umma Kubra ta dakko Danta a airport cikin sabuwar motar Abba, Beauty murna kamar me amma a gidan sirikai ne wani abin ba dama,sai kallon juna suke ita da Mohsin kamar zasu cinye juna,suna magana da Ido,yaga ta Sha kyau,Abba yace mutanen Makkah dama yau suka je aka gyara ko Ina na gidanku gashi kayanta ko kunya duk ta kwashe ta Maida gidanku tana sa rai miji ya kusa dawowa sai ku tafi gidanku ai,dama haka ta dinga tafiya gyaran jiki duk sabo da Kai ake yi na sani,shuru nayi kawai ban nuna ma nasan Dan Kai ake yi ba,ta zaci wai ta kife ni,yau mun huta muma zan samu tattalin arzikina ya dawo,Mohsin yayi dariya ya zauna sun dade suna hira,sannan yaci abinci yayi Sallah,Kubra tace ga key din motarka normal an mata komai,ya karba,Abba yace ya labarin su kubri (Saman gada) da su dukkani(Kanti)? ya ka gane min idon takari a can ana korar su suna likewa? Mohsin yayi dariya sosai yace suna can Abba,yace ya Darul tauhid ka ga Darul Salam a Madina ko? ai Yan biyu ne Hotel din,ya su bakiya anje ziyara? Mohsin shi dai Yana ta dariya Abba a dole yasan ko Ina,shi burin Mohsin a tafi gida ya gana da matarsa da dansa,Amal taga Abbanta sai murna take dama taje hutu wajen Hanan mamanta Ranar Sunan Beauty yazo dai dai da auren Mufee da Haidar shagali kan shagali,Haidar yayi lefe na gani na fada. Maryam kuwa kanwar Annoor sai da ta Sha jinya me tsanani ta fita a hayyacinta sannan ta warke a hankali,taci bakar wahala,maganin duniya yaki yi mata aiki. Bayan ta warke a rame a kekashe tazo gidan Annoor suna Parlo suna kallon film ta shugo tare da zubewa a kasa ta fashe da kuka tana rokon gafara,Annoor Sam bai gane ta ba sai da tace Maryam ce Yaya baka gane ni ba,Annoor ya daka tsalle ya koma gefe Jikin Iman ya makale yace kece Maryam? tana hawaye tace nice,yace Allahu Akbar ko Dan wannan halin da kike ciki ai a yafe miki,na yafe miki,Iman tace ke kuwa ba Kya iya cin abinci haka? Sweet ka ganta sai hakoran kawai,skeleton a fili mun yafe miki duniya da lahira,tace na gode Allah ya saka da Alkhairi,yace Ameen ki daina fitowa haka ki boye kanki ki bari sai kin murmure Allah ya Baki lafiya jeki zamu zo gidan tace to ta mike iska na ibanta,yace zauna ki huta,Iman tace to Kinga dai duniya sai kiyi darasi,taje ta kawo mota abin ci da Sha,taci kadan,Annoor yace in zaki kici ki ci Nan ba wajen kunya bane Sai da ta gama tace zata tafi,ta fita waje Wanda dama driver ne ya kawota shi ya Maida ta tana Jin dadi sun yafe mata. Mero taji jiki tace yau sai dai a dauke ni yau ma ,ka gama ragargaza ni,yau na Sha wahala,yace sorry My Angel bari muyi wanka,Mero tace ka fara dai bani ragowar kaza ta naci da tea me zafi hadin Madara,dariya yayi ya mike ya kawo mata abinda ta bukata,ya shiga bata a baki tana korawa da shayi me kauri,gobe Kuma sai naci tsire, idan Allah ya amince jibi Kuma sai a siyo min nama me ruwa ruwa Shima ya Sha cabbage,Haneef yayi dariya yace za a siyo inshaallah,tace ya zama wajibi da yardar Allah,irin wannan wahala da naci ai sai da sinadari me kyau in ba haka ba sai na fara hakoran gaba,yau da kyar zanyi fitsari an min kaciya,Haneef Yana dariya a nutse yana bata tana lamushewa. Ayi hakuri da wannan naje wajen aiki ne. AsmaBaffa [3/9, 9:21 AM] AsmaBaffa: 🏫TANTIRIYA🏫 A GIDAN YARI BOOK 3 ~TAIMAKO~ 81-85 Official By AsmaBaffa SADAUKARWA NE GA AIDA MAMAN TASNIM PAGE NAKI NE Yar Gatan Annabi Mohsin tun a mota Beauty take Masa korafi yanzu da ba'a gyara gidan ba fa? ai sai ka fada min,ni naga Umma tace Inzo muyi girki ana ta shirya girki na musamman Ina ta mamaki Ashe Kaine zaka dawo,surprise na miki, a'a ni bana so wlh ka daina min haka,sai da ya shiga gidan da motarsa ya rufe gate zata fito yace ki zamanki a mota a ciki zan bare sabuwar Amarya ta,Beauty tace ikon Allah mutum da bedroom da komai sai kace Yan iska,yace ba wani nan na gaji kullum Abu a daki,daga bedroom,Palo,toilet shike nan fa ai a dinga samun canji,yanzu wasu ma'auratan a duniya tunda aka aure su a waje Daya suke Abu daya,wasu basu taba barin bedroom ba,kullum a waje daya ba chanji,ai yanzu ma zamu fara yawace yawacen mu gari gari ko ba kudin fita waje ko su Lagos ai ma dinga zuwa,ga su Kwara state mu kwara kauna a can,Beauty tayi dariya yace ai kune wasu mata bama Kwa so a fita da ku,mijinki Yana da Dan budi ko katsina ai Kwaje kawai aci Aya ayi kauna,Beauty tace ai ni kasan ko nan da inane zanje indai da Kai,suka ajiye Baby a gaban mota suka shige bayan mota kamar Yan iska mota sai Lilo take a compound suna Kwalbewa. Ranar Sunan Chika Yana zuwa yarta taci Suna Nasreen,an Sha suna anyi shagali. Naila ana kan gaba har da wani Dj suka kawo sabo da bikin Mufee da Haidar, Iyalan Jauro Maza Abuja suka taho daurin aure,abokan Ango,Mohsin da Abba duk sun zo,Naila tayi tayi su Abba su kwana sun ki,Mohsin ya kawo mata tsaraba sosai,Chika ma an bata da Ikhy Abaya,harda kawowa Spark jallabiya kala biyu masu tsadar gaske fara da coffee color da turare me kyau. Washe gari aka Kai Amarya Mufee hadadden gidanta kusa da su Iman abinsu sharr, su Iman sune masu tabbar Amarya gaba dayansu yara da su,bayan mutane sun watse Haidar Allah Allah yake ya fada dakin Amaryarsa,ga Mufee Jinin su Zeenatu ba wata kunya ce da ita ba,tayi tunanin wani dadi ne da first night din. Sai da Haidar yazo suka gabatar da duk wani abubuwa na farkon aure sannan ya goge mata hadda gaba daya,Yar rashin kunyarta data kwaso daga Abuja duk ta Maida abarta cikinta ta hadiye,sai dai bata Sha wahala irin wasu ba,ba yanda ake tsammani ba,washe gari ma da kanta tayi komai tayi girki abinta,Mufee an dage an koyi girki kafin aure,Haidar har wani Santi yake yace daga Jin wannan girkin na tsohon hannu ne tun kina karama kike koyon girki? Mufee ta shararo karya tace ai mu tun muna Yan yara Mima take siyo mana Yan tukwane na yara muna gwada girki,tun muna yin na wasa har muzo ta kaimu kitchen,tana nuna mana zuba Maggi kaza,zuba curry,zuba gishiri kamar haka"a haka har a fara barin mu muna girki da kanmu abinmu. Haidar Yana Jin dadi Yana washe baki yace ai da gani Kun samu tarbiyya sosai,haka ake son iyaye,Mufee tayi dariya a ranta tace shiryuwa kawai muka yi muka ga rayuwa haka baza ta kaimu ko Ina ba muka canja,a fili Kuma tace gaskiya sai dai mu godewa Iyayenmu,Haidar yace bazan taba godewa nawa ba sai dai Kawu Jauro da Umma Habiba,suyi min laifi na gode musu a wanne dalili,Ina dai ganin girman su Ina mutunta su a matsayinsu na iyaye,Kuma bazan yarda wani ya wulakanta su ba amma na gode musu akan me,me suka yi na bajinta a kaina, Allah ya kyauta dai,Mufee tace Ameen ai ba laifin mama,yace to da sauki dai,dariya tayi suka koma hirarsu ta kauna. Bayan wasu watanni Naila cikinta ya tsufa sosai bata da karfin masifa yanzu sai kuka da fushi,yau da dare ta kasa kwanciya ta juya gefen dama taji bata Jin dadi,ta tashi zaune ta juya gefen hagu,Spark Yana ta latsa waya abinsa bai San ma tana yi ba Yana kwance a gefenta,Naila tace ayi bawa idan zai juya ma ba dama sai ya mike zaune kafin ma ya juya,da a baya ne sanda nake lafiya birgima nake yi harda kwanciyar banza amma yanzu idan na Isa nayi mana,Spark Yana jinta yayi murmushi bai ce komai ba,juyawa ta sake yi ta Kalli sama tace wayyo zan mutu ta mike ta jingina da Jikin gado sannan taji dadi,ta zauna a haka ta Kalli Spark haushi ya kamata ko sannu duk wahalar da take Sha,tace idan na haihu idan na kyaleka ka aiki yaron nan shegiya nake,wannan wanne irin Abu ne Allah yasa na haihu kazo daukansa bazan bayar ba,Kuma baza ka aike shi ba ko kofar gida,sai mace ta haihu ku damu mutane da Danku Danku akan me,sai an haihu ku zake kufi mata iko da yaran ku sai kace Kun San zafin su,Spark yace sannu yi hakuri,wayarsa ta kwace ta kashe gaba daya ta ajiyeta a gefe,hannun Spark ta jawo ta dora a Saman cikinta, yaji yaro Yana ta motsi a ciki ana ji,dariya yayi yace kin ji shi,Naila tace ae haka kuka iya ai dama,wlh watarana kamar na cinnawa kaina wuta haka nake ji sabo da halinka,na tsani kaina da kaina na gaji da cikin nan wlh ni bana so bazan sake haihuwa,ko na haihu nayi arba'in baza a kwalbe ba,duk dadinsa na hakura ai Kwalbewa ce ta jawo min,na damu kaina ban haihu ba ashe wahala ce bazan sake ba,Spark yayi dariya yace daga farawa ai kuwa na gaba Yan biyu ne zaki haifo Inshaallah,Naila ta fashe da kuka wlh bazan Haifa ba bana so,to kiji da wannan tukun yanzu tun baki samu na Yan biyun ba kike musu kuka? a guda daya ma Ina Jin haka Ina ga Yan biyu,a zaune tayi bacci Naila Allah sarki a jingine ta kwana,sai da Spark ya tausaya mata kamar ya mata kuka,ya dade baiyi bacci ba Yana kallonta tana bacci a haka. Kullum sai ta Kalli Edd dinta saura kwana nawa ya cika,sabo da halin da take ciki Spark bai fiye fita ba ma kullum suna tare Yana kula da ita,girki ma ba sosai take yi ba me aiki ke yi,yaran su Chika tuni sunyi wayo dagwas da su gwanin sha'awa. Naila tana fama Hanan itama ta haifi yarta mace Jibson sai murna akeyi shi da uwarsa suna ta Jin dadi. Basma dai ita shuru bata samu ciki ba suna ta soyewa ta Saba yanzu da harka. Mima ganin irin wahalar da Naila take Sha tace a dawo da ita gidanta Spark yace shi a'a zai kula da abarsa ta hakura ta bar Masa matarsa kawai. Naila ranar da Edd ya cika da sassafe ta tashi wai Nakuda take jira,tace Spark ka tsaya a kusa da naji kyas zamu tafi asibiti,basu San nakuda ba yace bari a fadawa Su Mima su zauna cikin shiri,duk ya kira waya ya fadawa har su Chika,Mima ya kira ku zauna cikin shiri Edd ya cika yau muna Nan muna jira tun jiya Sha biyun dare muke idon mu biyu muna jira ta fado,Mima tayi dariya kamar cikinta zai ciwon tace sai kace zuwan Christmas ko new year da ake cewa 12am na yi na dare ta Fado,Allah ya kawo me sauki,Naila tana gefensa tace duk kayan haihuwar na hada su abinda tace a hada duk an hada,Spark yace to kinji komai mun hada. Naila tana zaune shuru shuru tace bari naje toilet na gani ko irin ruwan Nan na haihuwa ya fara,taje ta duba ba komai ta cire pant dinta ta dawo haka ba pant sai rigarta doguwa me Fadi ta material ta zauna,can anjima tace bari muga wajen ya fara budewa ta bude riga ta leka Bado tace da saura,Spark yace mu gani zan fiki iya ganewa,ya bude ya gani daga leka Kai yaki fitowa,yace mu Kwalbe inyi last please,Naila ana murna yau fa tace ai kuwa a lallaba ayi, kayi a hankali yanda kake min dai na me tsohon ciki,yace ai sai da na Kara koya sosai. Remote ya danna kawai ya sawa kofar lock ,Yana Murza boobs din Naila yace gaskiya sun tunbatsa Baby kawai suke jira abin su,a nan suka kwalbe abinsu suka yi bacci a Saman carpet an manta da jiran haihuwa sai 2pm suka tashi sannan suka yi wanka tare da gabatar da Sallah,yamma tayi likis ba haihuwa ba alamunta,Naila ta fara zazzagin computer shegiya computer makaryaciya,dama idan aka ce Abu ba fadar Allah da Manzo ba bace to karka yarda zai iya karya. Da dare shuru suka sake Kwalbewa dai,washe gari shuru har an shole da asuba,duk Spark ne yake yin na bankwana,haka aka yini wani daren yazo ba haihuwa. Naila sai murna ta koma ciki Kuma ta dawo Boss dinta sai kuka sai masifa. Abba ya kira ta waya ya gaji da complain daga wayar yayi tace hello Abba yace the number does not exist please check the number and dial again,Naila tayi dariya kamar ba gobe Kuma ya fuske ya kashe wayarsa,mamakin Naila Ina Abba ya Iya turancin ma da zai ce haka,Umma ta kira ta Bata labari,Kubra tace Nan yasa Zarah ta dinga koya Masa wai idan number ta daina aiki ya MTN suke cewa,Inda kisan me haddar karatun Qur'ani ya Dade kafin ya iya kullum Kalma Daya ake biya Masa har ya iya Ashe ke yake wa tanadi,kin dame shi da complain,kin San in ya gaji da complain ko zuwa gidan Nan kika yi sai ya buya gwara ma ki daina in kina son zaman lafiya da mahaifinku,Naila tana ta dariya har Spark ya fito a Waka ta bashi Labari,Shima dariya yayi yace an gaji dake to. Kwana uku da cikar Edd din Naila,yau dai tun safe take Jin yanayi marar dadi ta kasa sukuni Sam,Bata kawo haihuwa bace,sai da ta zauna Zata tashi kenan taji ta kasa,Spark ta shiga kwalawa kira,ya fito da sauri tace na kasa tashi wlh,ya koma ya tattaro kayan haihuwar a Yar jaka me shegen kyau wai su Yan gayu ya sa mata Hijab ta fige ta jefar kanta ba dankwali a haka suka tafi asibiti,yace ko a kira Umman ki da Abba? Naila tace a'a kyale su kar hankalinsu ya tashiiiiiiiii....ta cije baki,Yana driving yace ki dinga salati kinji kina Kiran Sunan Allah, da sunanka zan kira,nace sunanka zan kira? Spark yace yi hakuri,karka sake bani hakuri bana so...sannu to....a haka suka je asibiti,already ya kira Mima,tazo ita da Chika da Ikhy,Naila ana labour room ana fama. Nurse tazo da iyayi tana cewa ai da sauran lokaci ma akwai gumurzu a gaba,Naila ta yanka mata Mari ta shake ta tana cewa duk wannan azabar da nake Sha kice ba yanzu ba inji ubanki,aka kwaci nurse da kyar,gata yarinya Yar budurwa wata Yar mummuna me dama dama,Nurse dafe da kumatu tace wlh sai na rama Allah ya kaimu ki haihu lafiya,wlh sai na rama,Naila tuni ma bata San tayi ba,Mima tace kiyi hakuri kece yarinya ce baki San ba a zuwa Jikin me nakuda a daga mata hankali ba,nakuda hauka ce Inji nurse ta fice wajen Spark dake waje Yana kaiwa da kawowa,tace Kaine mijinta ko wlh idan matarka ta haihu sai na rama marina da tayi,kawai daga zuwa sai ta shake ni ta mare ni,nakuda hauka ce,wlh tana haihuwa sai na rama,Spark yace wuce ko na Kara miki uku kaga Yar iskar Kwaila in da nasan kece ma zaki je kan matata ki tsaya wlh bazan kawota wannan asibitin ba,so kike a haifo min yata ko Dana kamarki,in macece ki jawo min karbo mata rubutu domin ke sai kafin ki auru sai an karbo miki rubutu,nurse zata yi magana yace kina magana zanyi ball Dake a wajen Nan naga me tsaya miki,kin kalle min Bado Allah ya isa,idonki kadai ya isa yasa Badon ya rage zaki,kar wata nurse wata Yar iska me kambun Ido ta kallar min tsaraicin matata ta cuceni,duk gyaran duniya yaki dawowa dai dai,Nurse dai taji Spark ya fita iskanci Dan tijara ne tayi gaba tana jira Naila ta haihu tazo ta mareta. Spark dakin ya leka ta window yace Mima karanta mata falaki da Nasi da suratul Iklass kafa uku uku,Mima ta zaci na neman saukin nakuda ne ta fara tana tofa mata a ciki yace ba a nan ba ta Inda zata haihu ta Saman riga ba cewa nayi ki daga mata riga ba,nidai naga ta kaina me yasa ma ba a kira Goggo ba,ace sirika Taga wajen Danta ni ban yarda da wannan tsarin ba,Maman Rafeeq yaje ya dakko tun daga gida ya kawota,gashi asibitin mace daya ce zata shiga wajen marar lafiya,haka yasa Mima ta fito Maman Rafeeq ta shiga,ya sake lekawa yace bakinki kanin kafar ki kar naji kar na gani kin Fadi wani Abu akan palace dina,Maman Rafeeq tace kaima haka kake Ashe irin Arham ne mudai mun shiga uku da jarabar yara. Sai da ya kira Goggo a waya yace ta taho kawai,Goggo dama Jira take ana kauye an hadawa Naila kayan gyara in ta haihu za a taho Abuja a kula da ita,yace ki zauna yanzu zan sa Azo a taho dake,Shaheed ya biyawa flight Dana Goggo yaje ta Kano yafi kusa sannan ya hau mota drop har kauyen ya dakko Goggo da kayanta suka dawo ta airport suka shiga jirgi Dan lokaci kankani sai gasu a Abuja,Goggo kayanta ta ajiye a gidan Naila sannan Shaheed ya taho da ita asibitin,tana zuwa Spark yace Maman Rafeeq fito wata kusan tafi wata kusan,Kakar ta tazo da kanta ba sako ba,Maman Rafeeq ta tabe baki tace na huta,dama halinku ya isheni,ta fito Goggo suka gaggaisa da su Mima tace Allah ya raba lafiya ta shiga ciki. Mima suna zaune suna hararar Spark wai ya musu rashin kunya,su Chika suna ta yiwa Naila addua sunyi jugum jugum,Spark sai yanzu yasan ya tambaya yaji haihuwa da wahala,ya Kalli Chika yace wai da wahala ne haka,Chika tace la'ilahaillahu ai mutuwa ce da kanta,Ikhy tace azaba kenan bana marmari yanzu tuni muka yi planning bamu sakewa da wuri Inshaallah,Spark ya sake rudewa ko Sallah ya kasa yi sai da kyar,har dare shuru har yayi Sallar Isha shuru Yana ta addua, Ma'aikatan lafiya suna ta Bada agaji sosai,Naila aka ce tayi Nishi tace karfina ya kare bazan iya ba wlh,Goggo tace in zaki yi kiyi,Naila tace mutuwa zanyi,Spark zama yayi a kujera Dan kafarsa baza ta iya daukansa ba,sai ya fara hawaye tun Yana Yar kwallarsa a boye har ya kasa boyewa,ba sauti sai hawaye,Mima tazo tana lallashinsa tace zata haihu lafiya inshaallah ka daina damuwa duk haka muka yi muma,Spark yace wlh da nasan haka ne da banyi cikin nan ba,gwara ma kar nayi komai to kaddara da rabon za ayi haka,sai da ya basu dariya gaba daya har mutanen wajen da suke jinsu. Can yaji Naila tana wani irin Nishi tana gurnani kamar zata mutu,sai Kuma yaji kukan jariri ko murna baiyi ba shi dai Yaya Naila,Naila tana haihuwa ta daina gani sai a hankali ta farfado a hankali ta dawo hayyacinta,ta haihu lafiya komai ta gama shi lokaci guda babu wani jiran komai,Namiji ta haifo katon gaske sai yayi kama biyu shi ba Naila ba shi ba Spark ba haka yake,Spark yaji dai Muryar Naila tana cewa Goggo Alhmdllh nuna min shi,Ashe zan iya haihuwa,sai lokacin Spark yaji salama,Dan windon da yake lekawa sun rufe abinsu tuni sabo da ya dame su da leke tun farkon kawota. Mima suna Murna suka ce Alhmdllh da lafiya ma Inshaallah,Sai da aka yiwa Naila duk abinda ya dace da Allurai da komai suka cire mata Jinin mararta,ga Allura taji karfi a jikinta Goggo ta sa tayi wanka a toilet din,Dake asibitin na manya ne kamar kana gidanka ko Ina kamshi,haka tayi wanka da sabulu me kamshi tace kayan da suka baci a zubar,Goggo tace baki isa ba tana fitowa aka canja mata daki bayan Goggo ta wanke kayan da suka Baci,babu ma abinda ta bata sai iya rigar jikinta,Naila ta shirya kanta tace da kyar nake Shirin Nan iska daukana take sai naji bani da nauyi,Goggo tace ai kin samu me sauki wlh kin haihu lafiya wata ai bata Isa ta iya tashi yanzu ba,Naila tace Chika sai da ta kwana ma sannan ta iya yin wanka. Jariri Yana nade a cikin showel fari aka sa masa kayansa farare tas da shi Yana ta baccinsa. Spark ya matsu yaga Nailansa amma Goggo ta hana shiga sai sun shirya. Naila tunda ta canja kaya ta zura Abaya da wondonta dogo bayan ta shirya kanta ta kwanta bacci na son yin gaba da ita ga wahalar haihuwa,daga haihuwa ai baka isa kaji dai dai ba. Goggo ce tace ta fito daga wani dakin ta kofar baya ashe aka canja musu room,ta tako da Dan Nisa tace muna Nan fa kuzo kuga jariri da Me jego an haihu lafiya anyi arziki,Spark ne a gaba ya wuce Goggo tace har tayi wanka fa yanzu abinci nake so taci kafin ta huta,Spark yace yanzu za a kawo ai,suna shiga ciki suka hada Ido da Naila Dake kwance,suka sakarwa juna murmushi harda wani signa da Ido wai su sunyi Da,Mima ta karbi jariri tana cewa Masha Allah lallai an samu Karuwa,Naila tace Allah ya nufa,Goggo ta make ta tace ku ko kunyar Dan fari bakya ji a gaban sirika,Maman Rafeeq tace Allah ya raya bisa sunna,Naila tace Goggo nace Ameen?nidai zance Ameen ai addua ce,dariya aka yi Spark yace Allahumma Ameen,Spark ya Kalli Naila duk har ta canja da Gani ta Sha wahala,hannu ya mika mata Yana zaune a gefen bed din ta saka nata ciki,yace sannu kin Sha wahala,Finally dai an haihu na huta da cizo da kuka da masifa,Naila tayi dariya tace kunya ma nake ji yanzu in na tuna,yanzu me kike so? Cikinta ta nuna Masa tace yunwa kamar zanyi me a bani abinci Dan Allah,Arham ne ya shugo tare da Basma da flask wurin kala hudu na abinci daban daban,ga take away Kuma da Spark yace ya taho da shi na fruits da nama me ruwa ruwa, yogurt da sauransu,shayi aka hada mata lafiyayye ta mike zaune Spark Yana Bata a Baki sauran suna ta hirar su,Maman Rafeeq ta Kalli Arham taga ya juya can wai gyara mata adon rigarta yake bayan adon a Saman Boobs dinta suke,rankwashi ta zuba Masa tace Kai dai Allah wadaran halinka,nifa Mima gaba daya yaron nan naki ya kwance min Dan iska fitsararre,Arham yayi dariya yace idan kishi kike yi kawo na gyara miki kema gashi Nan an miki tuta a wajen ai,yaron ya karba Yana Masa addua,Maman Rafeeq tace Allah yasa adduarka tayi Masa aiki badalallen yaro,Mima tayi dariya tace kin da damar min yaro Dan kinje gidansa ya Koro ki sai ki dame shi,Arham yace gani tayi ana soyayyar da ita a zamaninsu babu irinta shine take kishi,Maman Rafeeq tace kaji min yaro ni da mijina yake Dan Sudan mene bai sani ba,har ka fadawa Balarabe kauna. Naila tana shanye shayi da nama kadan ta rage Naman,ta koma kan faten doya da wake taci taci ta koshi ta Sha fruits da ruwa ta Dan huta sannan ta kwanta sai bacci,tun dare sai washe gari da rana ma aka sallame su,Mima a motarta ta wuce da Naila da Goggon gidanta direct,Naila tasan Spark Bai sani ba ta dai yi shuru,sai da yaje gida shi yaga ba nan aka kawota ba,ya nufi gidan Mima Yana cewa ai dalilin dakko Goggo kenan tazo ta zauna da Naila. Mima tace to ai na sani Malam ka bari dai ta huta ,yace shi wlh a'a,Goggo tace ka bari tayi wanka sosai ta gasa jikinta ayiwa Jaririn sai mu tafi,yace yawwa,Spark tunda ya dauki Jaririn ya Masa addua bai Kuma daukansa ba Yana hannun Yan uwa har so yake a ajiye shi ya dauki abinsa amma daga hannun wannan sai ya fada hannun wannan. Nurse me jiran Naila ta haihu ta rama Marinta lokacin tashinta yayi amma jira take taki tafiya sai Naila ta haihu,tana can ta kwanta tayi bacci sai da me asibitin yazo ya dinga fada Dan me Bata tafi ba ya Kore ta gida,tace wlh Allah ya hada mu watarana a hanya ai na gane ta. Naila wanka tayi Goggo ce da kanta tayi mata gashi,Naila har hawaye tayi ta Sha wahala a hannun Goggo da gashin towel,an zuba gishiri a ruwan sabo da kashe wasu kwayoyin cutar,Sai da ta gama Naila tasa shampoo ta wanke gashinta sosai sai kamshi ke tashi,tayi wanka da sabulu ta fito,Mima tayiwa Jariri wanka tas an canja Masa kaya,kayan Naila na asibiti duk da Goggo ta wanke Spark gaba daya ya kwashe ya zuba a washing machine ya sake wanke su,ya zuba na jariri ma ya wanke tas suna kamshi ya tattara a cikin bahon jariri ko kunya,ya saka a mota yazo duk ya kwashe abinda suka zo da shi kaf ya Kai motarsa,Naila ta saka kaya tana daure gashinta da ribbon gashinta yanzu yayi mugun tsayi Dake Jinin gashi ce har ya dawo bayan uwar daadaa da yasha a gidan yari. Mima wani abincin ta shirya musu suka tafi da shi a mota tace ala raka taki gona ta fadawa Spark yayi dariya yace Ameen,zasu shiga mota Papa yazo ya dawo yazo ya dauki jariri ya Masa addua ya yiwa Naila murna,Spark yace sai fa kazo har gida Papa ban karbi wannan ba,Misam da Rafeeq har gida kaje ganin jariri Nima sai kazo,Papa yayi dariya yace zanzo Inshaallah,na Arham dai in za a haihu har asibiti zanje,dariya suka yi har Arham Dake ya fito shi da Basma zasu tafi,shi yasa Papa yayi zancen ma,Arham yace Allah ya kaimu,ai Bata da ciki wata nawa Amarcina nake Sha kawai ai haka yafi,Papa yace Allah ya bada na gari,yace Ameen yaushe zaka zo muyi hira ne?Papa yace sabo da yana son yayi hira da Spark da Arham,in suka zo ko banza yayi dariya,Rafeeq shi in yaga dama ma yaji yake ya daina zuwa,Misam ma basu Shaku ba,in yazo ma basa hira, Arham yayi dariya yace yau ma dan na gaji ne amma da tuni na zance ka da magana sai na dawo zanzo weekend ai Papa Soja sarkin fara'a,irin wai yasan baya fara'a sosai shine yace sarkin fara'a,Basma tace Papa mun tafi yanzu munyi hankali,Yace to Basma Haka ake so ayi ta hankali,tace to suka tafi, Papa yace a ransa Ina kuka ga wani hankali ai sai dai gaba kuyi hankali tare. Naila tun a mota ta kira Yan uwa ta fada musu,Mohsin ta fara fadawa,ta fadawa Umma ,ta kira wayar Abba sai da yaji ance ta haihu ya daga wayar Yana murna,tace Abba na haihu,yace Inyee su Naila an girma za a fara koya tarbiyya,Allah ya raya bisa sunna tace Ameen,yace yawwa karki biyewa su Goggo da kauyenci baza a amsa addua ba, kowa yace Allah ya raya kice Ameen, kanki tsaye ki amsa Ameen idan ance kinyi fitsara kice ni na saki kakan yaro ne,Naila tace Nima dai shine na Gani,yace yawwa karki yarda da kauyencin su Goggo,Sannan karki matsawa mijinki da maganar kashe kudi akan kin haihu nasan ku mata in kuka samu waje sai Kun Kai mutum bango ki bari duk abinda ya siya kiyi godiya,Naila tace ai dama Abba ai ba kullum ake kwana a gado ba,Abba da sauri yace a'a Banda ni" Naila kullum a gado nake kwana tun Ina jariri akan gado karami na babata ake dorani" babata Kuma da Mijinta babana kenan suna kan babban gado ni Ina karamin gado,har na girma aka mayar min da gadona dakina gashi har na auri Yar Inna yau shekaru kusan arba'in ban taba fashin kwana akan gado ba,Naila tace gaskiya ne tana murmushi,yace sai bayan suna zamu zo da Yar Inna,su Hidaya dai da su Zarah zasu zo kafin suna,tace to Allah ya kaimu. Suna komawa gida Naila tace yunwa nake ji da bacci,Spark wanka ya shiga yayi wanka sosai ya fito tare da saka sabuwar jallabiyarsa da Mohsin ya kawo Masa,Naila a dakinta Goggo ta sake yi mata wankan yamma,bata shirya ba sai da taci abinci dare yayi sannan kaya ta sake canjawa ta saka rigar baccinta doguwa me kyau me gajeren hannu Orange color, Goggo tace sai an daure ciki,Naila tasa abin daure ciki na Yan gayu Wanda a kasar waje ma aka siyo mata kala nawa da kyar ake matse ciki da shi na rage girman ciki,sai da ta saka sannan ta shafa turaruka ta Maida rigar Baccin kamar ba ta sa komai ba ciki ya lafe ya dame. Goggo ma wanka tayi ta fito ta hau Naila da fada yanzu dama da nace ki bashi nono Baki bashi ba? tunda aka haife shi sau daya kika bashi nono sai zam zam kawai aka bashi fa,wannan wacce mugunta ce,boyon nono ya kare yarinya cewar Goggo,Naila ta dauki Jaririn Yana ta cin hannu Yana zare Ido, Goggo tace tsaya na koya miki yanda ake yi,sai da ta koyawa Naila sannan tace to kiyi Bismillah,Naila tayi Bismillah ta juya baya ta fara bashi wai Goggo baza ta kallar mata nono ba,Goggo tace a gaban mu fa kika yi nono har ya girma me zaki boye min shashasha,naga dazu ni nayi miki wanka,Naila tace naji ga Abinci nan Goggo ki ebi abinda kike so,Goggo tace mijin naki fa? Na zuba Masa nasa kina wanka na Kai Masa,Goggo tace Iyye kaji kula da miji,dariya Naila tayi,Naila bayan ya Sha daya ta juya shi yanda Goggo tace ta bashi dayan,Yana Sha Goggo tace ai ya koshi haka,to rike shi a hankali karki hantsila shi zaiyi amai,Naila tace Kai wannan yaro haba ace wannan ace waccen,sai da ya huta tace bari na kaiwa Daddyn sa shi ya ganshi,Goggo tace kwaji da shi munafukan banza wlh ki dawo a nan zaki kwana,Naila tace to,ta fice da danta cikin showel ta shiga dakin Spark Yana cin abinci Yana kallo ta shigo Ya kalleta Yana Jin dadi a ransa yace fada ya kare tace ae mana,kallonta ya sake yi yace wai dama idan an haihu kyau ake yi ne? duk naga in kuka haihu sai mace tayi wani kyau fatarta tana shining,Naila tace ai haka yawanci ake yi sai zuwa arba'in ake dawowa normal,Naila ta juyo fuskar jariri tace ka ganshi fa Kaine babansa Kai ka haifi wannan,Spark yace duniya sabuwa SparkNaila kamanninsa biyu,Naila tace Nima haka nace kamanninsa biyu,sai da ya gama cin abincinsa ya dauke shi,wanne suna za a sa Masa ne? Naila tace oho ka zaba,Spark yace Papa Ahmad in yayi miki a saka idan kina da zabi ki zaba,tace a'a Banda da zabi Kuma ai suna me dadi ne na kololuwa Ahmad fa,Allah ka raya Ahmad bisa sunna,Allah kayi Masa Albarka kasa ya zama mahaddacin Alqur'ani,Allah kasa yayi koyi da fiyayyen halitta Annabi Muhammad (SAW),Allah kasa duniya ta amfane shi,muma iyayensa ya amfane mu ya zame mana Alkhairi dukkanmu da Yan uwa da Al'ummar musulmai Baki daya,Allah yasa yayi suna ta hanya me kyau,ya shahara a duniya ta hanya me kyau,ba shaharar Dan Boko Haram ba,Bata Dan kidnapping ba,Bata Dan daba ko wani Dan iska ba,shahara ta hanyar abin Alkhairi,Allah yasa Shahidi ne,Allah ya Masa Albarka,Wannan Dan nawa Ahmad Allah ya sa Masa Albarka,Allah ya bashi lafiya da tsawon rai,Allah ya azurta shi ya raba shi da talauci,Allah yasa Dan Aljanna ne,Allah ya bashi mata ta gari Irina kyakyawa,Spark Yana ta amsawa da Ameen Ameen Yana dariya yanda Naila ta dage take surfa addua ta daga yaro sama tana cewa Allah ga Dana Ahmad,Allah ga Dana Ahmad,ya Rab ya Rab,ya Rab ka amsa addua ta. Tana gamawa Spark yace well-done uwa ta gari haka ake so wlh uwa ta fara yiwa danta,Shima ya karba yace kawo shi Nima nayi nawa Shima ya tallafe jariri ya Dan daga sama kadan ya fara zubo addua tana amsawa Ameen...Ameen..Ameen sai da suka gama sannan Spark yace yaushe zan dauke shi ne ya tsula min fitsari? Dariya Naila tayi,yace to ai ya kamata ace Danka ya Maka fitsari,Naila tace saurin me kake yi zaiyi ne ai bari a fara barin duwawunsa Yana hutawa ka gani,har Kashi ma zai Maka watarana,yace Ina maraba indai na dana nane,spark da baya daukan yaro amma shi yake neman fitsarin dansa yanzu. Naila ta dauki Baby tace bari naje sai da safe,sai da safe Ina?wai Ina bed din Baby ne,Goggo tace tare zamu na kwana,yace muje wajen Goggon ni zan mata bayani akan mene haka zamanin da ne wannan. Spark tashi yayi suka tafi da Naila yayi yayi akan Goggo ta fahimta amma Goggo taki yarda,fita yayi Dan yaji haushi,Naila tace Kinga yaji haushi in haka ne mene amfanin yace bazan zauna a wajen Mima ba,wlh ba wani Abu zai min ba,kin sani kema ba halin yin komai,sabo da haka yasa aka taho dake,kullum muna tare dake da jaririn ace bazan kwana a can ba,Goggo tace wlh bari na kira uwarki na fada mata tunda baki da kunya tafiya zanyi,Naila ta kwanta a gadon ta ajiye Baby a gefenta,Spark shi kadai ya kwana ya hakura Kuma da safe ma bai ce komai ba bai nuna fushi ba ko a fuska har wasa suka yi da Goggo,washe gari haka Goggo tayi komai na gidan ta gyara ko Ina ta kula da Naila da Baby,girki me aiki tayi,haka Naila ta sake kwana da Baby da Goggo har kwana uku,kwana na ukun ta kira Abba a boye ta fada Masa,Abba yace kyaleta bari na kira ta,Abba ya kira Goggo ta daga waya,yace wanne dalilin zaki je ki Hana su sakewa daga ganin sarkin fawa sai Miya tayi zaki,birni ba haka ake yi ba yanzu,ki kyale yarinya,Goggo tace so take ayi mata wani cikin da wuri,ayi mata mana ke Ina ruwanki a jikinki yake,ana ta murna a kira Goggo sai kizo ki watsawa mijinta kasa a Ido ki kyaleta,iya aikinki kiyi Dan Allah. Goggo tace shike nan tunda ku birni Kun lalace babu kunya taje ta kwana,idan yaro Yana kuka ai tayi sintiri a hanya zuwa dakina, yace ba komai tayi sintirin ya kashe wayarsa. Naila tana shugowa Goggo tace munafuka har da fadawa ubanki kije kiyi ta kwana ai mayyar miji,dariya Naila tayi tace naji. Yau da dare bayan Yan barka sun tafi tayi wankanta ta saka riga da wando blue na bacci ta Sha kyau ta dauki Danta ta yiwa Goggo sai da safe,ta shiga bedroom din Spark,baiyi tunanin kwana zata yi ba,yace Goggo ta ishe ni da nasan haka ne bazan kawo ta ba wlh,Naila ta fara hada gadon Baby a gefen nasu hadadden bed fari tas da shi,Spark yace ta yarda ne ki kwana? Naila tace tun yaushe na fadawa Abba ya kira ta a waya kuwa yace ba ruwanta da mu,Spark yaji dadi yace yawwa tsohuwa ta ishe ni haba,Naila tayi dariya ya dauki Baby,yace yaron nan ya bani wahala kafin yazo duniya,Naila ta bashi nono ya Sha ta kwantar da shi. Yayin da Maryam kanwar Annoor ta samu miji bayan ta murmure tayi aure abinta itama,suna ta zumuncinsu da Annoor. Ihsan tana yin Idda ta samu saurayinta da take so tace tana sonsa bayan ta bashi jari ya kama business babba,ta kashe Masa mugun kudi,ta siya Masa mota bai taba cewa Yana sonta ba sai dai ya nuna shi kawai birge shi take yi,tun tana jira yace Yana sonta har ta gaji ta fada Masa da kanta,kowa ya gansu zai ce masoya ne yanda suke mu'amula,suke waya,yake zuwa gidanta da sauran su,yaci kudinta matuka,Ashe shi Yana kama kasa ya koma wajen Tsohuwar budurwarsa da aka hanashi sabo da baida sana'a Yana komawa aka ce ya turo Kuma ya Kai kudin aure,a ransa tayi tunanin ko ya auri Ihsan din sai yaga tafi karfinsa ita tana da kudi baza ta juyu a wajensa ba kawai ya nemi dai dai shi,sai da Ihsan tace tana sonsa yace ai shi an saka ranarsa da wata,Ihsan ga aji tace ba komai ba damuwa kamar gaske ta nuna bata damu ba, Ashe Kara ta shigar kotu ta kashe Masa kudinta ya yaudare ta zai auri wata. Sai da suka je kotu sannan ma yaji labari ta taba aure duk lokacin da take kulashi tana da aure,Nan yayiwa Allah godiya da bai aure ta ba, Alkali yaji ma kudin ba roka yayi ba babu manufa kawai ta dinga kashe Masa kudi,Alkali yace ficika bazai biyaki ba tunda yarjejeniya kuka yi ba,haka kawai kika bashi kyauta Kuma kin amsa,Ihsan tace Dan me bazai gane sonsa nake ba shi Dabba ne,Sadeeq me kurkura yace nasan gaibu ne ni da zan gane,Alkhali ya dakatar da su yace Allah ya azurta Sadeeq ta hanyarki,ki hakura ki nemi ladan Allah sai Allah ya baki wani na gari,Ihsan tace ni ban yarda ba,Alkali ya Kori Kara yayi rubutu matukar ta takurawa me kurkura sai an yanke mata hukunci,Ihsan ba nasara ta rasa Inda zata sa kanta gashi ta bari an sake ta,gidanta na Kano ta dawo ta kwana tana kuka da Dana sani,washe gari da safe ta nufi gidan Haneef. Gidan ta gani komai ya canja ya Kara haduwa,sababbin motoci ba Wanda ta sani ba,ta danna door bell,ba a Dade ba Khadija ta bude kofar wow,ta zama wata Yar gayu da ita,ta Kara kiba da haske ta zuba kyau cikin kana Nan kaya,Ihsan mamaki ya kamata kamar ba Khadija ba,fuska ta bata tace uban me kike a gidan nan har yanzu,Khadija tace ubanki nake yi,an sake ki me ya kawo ki nan gantalalliya,Khadija ta kalla sosai taga ciki a jikinta bakin ciki ya tokare Ihsan a makoshi,Honey Mero ta shiga kwalawa kira ya fito yana cewa na'am Beb,yaga Ihsan da mamaki yace ke me ya kawo ki ya bata rai,Ihsan tace Baby Dan Allah kayi hakuri,Babyn ubanki dalla fitar min a gida,rungume Haneef zata yi Khadija ta fyalle mata Mari, tace dama haushinki nake ji an sakeki ban sani ba,Haneef yace fitar min a gidana Ihsan,ni kake kora Haneef Ina Yar uwarka yace an Kore ki,karki zubarwa da matata ciki da fada,ya fisgi Hannun Ihsan ya bude kofa tare da jefata waje ya kulle kofarsa,Mero ta harda goge masa hannu hannu kamar ya taba Kashi ta goge masa tace muje. Haneef ya dakkowa Mero me koya mata karatun Boko tana yi sosai sannan zata zana waec Nan gaba ya sata a makaranta,gashi ya siyawa Jummai gida madaidaici a birni tare da danta Mummir,ya saka Munnir a makaranta sannan ya bude Musu katon shagon cosmetics,Munnir Yana juyawa,Jummai tana siyar da kayan kanti shago guda ya mata a gidan,abinci da komai basu rasa ba,sannan da su za ayi aikin hajji badi harda Mero da shi zasu tafi gaba dayan su. Mero tace ya kamata naje har gida na gaida Spark da su Mima suga ci gabana,sannan naje prison na nunawa Mummy da tace ban dace da suna Khadija ba sai dai Mero,Ina ji ina Gani ta rada min Mero,sabo da banyi Ilimin Boko ba bamu da kudi mu Yan kauye ne,gashi yau ita ta kare mata ni Kuma Allah ya daga ni,Haneef yace ya kamata kuwa muje gaskiya. [3/9, 9:38 AM] AsmaBaffa: 🏫TANTIRIYA🏫 A GIDAN YARI BOOK 3 ~TAIMAKO~ 81-90 Official By AsmaBaffa SADAUKARWA NE GA AIDA MAMAN TASNIM PAGE NAKI NE Yar Gatan Annabi Mohsin tun a mota Beauty take Masa korafi yanzu da ba'a gyara gidan ba fa? ai sai ka fada min,ni naga Umma tace Inzo muyi girki ana ta shirya girki na musamman Ina ta mamaki Ashe Kaine zaka dawo,surprise na miki, a'a ni bana so wlh ka daina min haka,sai da ya shiga gidan da motarsa ya rufe gate zata fito yace ki zamanki a mota a ciki zan bare sabuwar Amarya ta,Beauty tace ikon Allah mutum da bedroom da komai sai kace Yan iska,yace ba wani nan na gaji kullum Abu a daki,daga bedroom,Palo,toilet shike nan fa ai a dinga samun canji,yanzu wasu ma'auratan a duniya tunda aka aure su a waje Daya suke Abu daya,wasu basu taba barin bedroom ba,kullum a waje daya ba chanji,ai yanzu ma zamu fara yawace yawacen mu gari gari ko ba kudin fita waje ko su Lagos ai ma dinga zuwa,ga su Kwara state mu kwara kauna a can,Beauty tayi dariya yace ai kune wasu mata bama Kwa so a fita da ku,mijinki Yana da Dan budi ko katsina ai Kwaje kawai aci Aya ayi kauna,Beauty tace ai ni kasan ko nan da inane zanje indai da Kai,suka ajiye Baby a gaban mota suka shige bayan mota kamar Yan iska mota sai Lilo take a compound suna Kwalbewa. Ranar Sunan Chika Yana zuwa yarta taci Suna Nasreen,an Sha suna anyi shagali. Naila ana kan gaba har da wani Dj suka kawo sabo da bikin Mufee da Haidar, Iyalan Jauro Maza Abuja suka taho daurin aure,abokan Ango,Mohsin da Abba duk sun zo,Naila tayi tayi su Abba su kwana sun ki,Mohsin ya kawo mata tsaraba sosai,Chika ma an bata da Ikhy Abaya,harda kawowa Spark jallabiya kala biyu masu tsadar gaske fara da coffee color da turare me kyau. Washe gari aka Kai Amarya Mufee hadadden gidanta kusa da su Iman abinsu sharr, su Iman sune masu tabbar Amarya gaba dayansu yara da su,bayan mutane sun watse Haidar Allah Allah yake ya fada dakin Amaryarsa,ga Mufee Jinin su Zeenatu ba wata kunya ce da ita ba,tayi tunanin wani dadi ne da first night din. Sai da Haidar yazo suka gabatar da duk wani abubuwa na farkon aure sannan ya goge mata hadda gaba daya,Yar rashin kunyarta data kwaso daga Abuja duk ta Maida abarta cikinta ta hadiye,sai dai bata Sha wahala irin wasu ba,ba yanda ake tsammani ba,washe gari ma da kanta tayi komai tayi girki abinta,Mufee an dage an koyi girki kafin aure,Haidar har wani Santi yake yace daga Jin wannan girkin na tsohon hannu ne tun kina karama kike koyon girki? Mufee ta shararo karya tace ai mu tun muna Yan yara Mima take siyo mana Yan tukwane na yara muna gwada girki,tun muna yin na wasa har muzo ta kaimu kitchen,tana nuna mana zuba Maggi kaza,zuba curry,zuba gishiri kamar haka"a haka har a fara barin mu muna girki da kanmu abinmu. Haidar Yana Jin dadi Yana washe baki yace ai da gani Kun samu tarbiyya sosai,haka ake son iyaye,Mufee tayi dariya a ranta tace shiryuwa kawai muka yi muka ga rayuwa haka baza ta kaimu ko Ina ba muka canja,a fili Kuma tace gaskiya sai dai mu godewa Iyayenmu,Haidar yace bazan taba godewa nawa ba sai dai Kawu Jauro da Umma Habiba,suyi min laifi na gode musu a wanne dalili,Ina dai ganin girman su Ina mutunta su a matsayinsu na iyaye,Kuma bazan yarda wani ya wulakanta su ba amma na gode musu akan me,me suka yi na bajinta a kaina, Allah ya kyauta dai,Mufee tace Ameen ai ba laifin mama,yace to da sauki dai,dariya tayi suka koma hirarsu ta kauna. Bayan wasu watanni Naila cikinta ya tsufa sosai bata da karfin masifa yanzu sai kuka da fushi,yau da dare ta kasa kwanciya ta juya gefen dama taji bata Jin dadi,ta tashi zaune ta juya gefen hagu,Spark Yana ta latsa waya abinsa bai San ma tana yi ba Yana kwance a gefenta,Naila tace ayi bawa idan zai juya ma ba dama sai ya mike zaune kafin ma ya juya,da a baya ne sanda nake lafiya birgima nake yi harda kwanciyar banza amma yanzu idan na Isa nayi mana,Spark Yana jinta yayi murmushi bai ce komai ba,juyawa ta sake yi ta Kalli sama tace wayyo zan mutu ta mike ta jingina da Jikin gado sannan taji dadi,ta zauna a haka ta Kalli Spark haushi ya kamata ko sannu duk wahalar da take Sha,tace idan na haihu idan na kyaleka ka aiki yaron nan shegiya nake,wannan wanne irin Abu ne Allah yasa na haihu kazo daukansa bazan bayar ba,Kuma baza ka aike shi ba ko kofar gida,sai mace ta haihu ku damu mutane da Danku Danku akan me,sai an haihu ku zake kufi mata iko da yaran ku sai kace Kun San zafin su,Spark yace sannu yi hakuri,wayarsa ta kwace ta kashe gaba daya ta ajiyeta a gefe,hannun Spark ta jawo ta dora a Saman cikinta, yaji yaro Yana ta motsi a ciki ana ji,dariya yayi yace kin ji shi,Naila tace ae haka kuka iya ai dama,wlh watarana kamar na cinnawa kaina wuta haka nake ji sabo da halinka,na tsani kaina da kaina na gaji da cikin nan wlh ni bana so bazan sake haihuwa,ko na haihu nayi arba'in baza a kwalbe ba,duk dadinsa na hakura ai Kwalbewa ce ta jawo min,na damu kaina ban haihu ba ashe wahala ce bazan sake ba,Spark yayi dariya yace daga farawa ai kuwa na gaba Yan biyu ne zaki haifo Inshaallah,Naila ta fashe da kuka wlh bazan Haifa ba bana so,to kiji da wannan tukun yanzu tun baki samu na Yan biyun ba kike musu kuka? a guda daya ma Ina Jin haka Ina ga Yan biyu,a zaune tayi bacci Naila Allah sarki a jingine ta kwana,sai da Spark ya tausaya mata kamar ya mata kuka,ya dade baiyi bacci ba Yana kallonta tana bacci a haka. Kullum sai ta Kalli Edd dinta saura kwana nawa ya cika,sabo da halin da take ciki Spark bai fiye fita ba ma kullum suna tare Yana kula da ita,girki ma ba sosai take yi ba me aiki ke yi,yaran su Chika tuni sunyi wayo dagwas da su gwanin sha'awa. Naila tana fama Hanan itama ta haifi yarta mace Jibson sai murna akeyi shi da uwarsa suna ta Jin dadi. Basma dai ita shuru bata samu ciki ba suna ta soyewa ta Saba yanzu da harka. Mima ganin irin wahalar da Naila take Sha tace a dawo da ita gidanta Spark yace shi a'a zai kula da abarsa ta hakura ta bar Masa matarsa kawai. Naila ranar da Edd ya cika da sassafe ta tashi wai Nakuda take jira,tace Spark ka tsaya a kusa da naji kyas zamu tafi asibiti,basu San nakuda ba yace bari a fadawa Su Mima su zauna cikin shiri,duk ya kira waya ya fadawa har su Chika,Mima ya kira ku zauna cikin shiri Edd ya cika yau muna Nan muna jira tun jiya Sha biyun dare muke idon mu biyu muna jira ta fado,Mima tayi dariya kamar cikinta zai ciwon tace sai kace zuwan Christmas ko new year da ake cewa 12am na yi na dare ta Fado,Allah ya kawo me sauki,Naila tana gefensa tace duk kayan haihuwar na hada su abinda tace a hada duk an hada,Spark yace to kinji komai mun hada. Naila tana zaune shuru shuru tace bari naje toilet na gani ko irin ruwan Nan na haihuwa ya fara,taje ta duba ba komai ta cire pant dinta ta dawo haka ba pant sai rigarta doguwa me Fadi ta material ta zauna,can anjima tace bari muga wajen ya fara budewa ta bude riga ta leka Bado tace da saura,Spark yace mu gani zan fiki iya ganewa,ya bude ya gani daga leka Kai yaki fitowa,yace mu Kwalbe inyi last please,Naila ana murna yau fa tace ai kuwa a lallaba ayi, kayi a hankali yanda kake min dai na me tsohon ciki,yace ai sai da na Kara koya sosai. Remote ya danna kawai ya sawa kofar lock ,Yana Murza boobs din Naila yace gaskiya sun tunbatsa Baby kawai suke jira abin su,a nan suka kwalbe abinsu suka yi bacci a Saman carpet an manta da jiran haihuwa sai 2pm suka tashi sannan suka yi wanka tare da gabatar da Sallah,yamma tayi likis ba haihuwa ba alamunta,Naila ta fara zazzagin computer shegiya computer makaryaciya,dama idan aka ce Abu ba fadar Allah da Manzo ba bace to karka yarda zai iya karya. Da dare shuru suka sake Kwalbewa dai,washe gari shuru har an shole da asuba,duk Spark ne yake yin na bankwana,haka aka yini wani daren yazo ba haihuwa. Naila sai murna ta koma ciki Kuma ta dawo Boss dinta sai kuka sai masifa. Abba ya kira ta waya ya gaji da complain daga wayar yayi tace hello Abba yace the number does not exist please check the number and dial again,Naila tayi dariya kamar ba gobe Kuma ya fuske ya kashe wayarsa,mamakin Naila Ina Abba ya Iya turancin ma da zai ce haka,Umma ta kira ta Bata labari,Kubra tace Nan yasa Zarah ta dinga koya Masa wai idan number ta daina aiki ya MTN suke cewa,Inda kisan me haddar karatun Qur'ani ya Dade kafin ya iya kullum Kalma Daya ake biya Masa har ya iya Ashe ke yake wa tanadi,kin dame shi da complain,kin San in ya gaji da complain ko zuwa gidan Nan kika yi sai ya buya gwara ma ki daina in kina son zaman lafiya da mahaifinku,Naila tana ta dariya har Spark ya fito a Waka ta bashi Labari,Shima dariya yayi yace an gaji dake to. Kwana uku da cikar Edd din Naila,yau dai tun safe take Jin yanayi marar dadi ta kasa sukuni Sam,Bata kawo haihuwa bace,sai da ta zauna Zata tashi kenan taji ta kasa,Spark ta shiga kwalawa kira,ya fito da sauri tace na kasa tashi wlh,ya koma ya tattaro kayan haihuwar a Yar jaka me shegen kyau wai su Yan gayu ya sa mata Hijab ta fige ta jefar kanta ba dankwali a haka suka tafi asibiti,yace ko a kira Umman ki da Abba? Naila tace a'a kyale su kar hankalinsu ya tashiiiiiiiii....ta cije baki,Yana driving yace ki dinga salati kinji kina Kiran Sunan Allah, da sunanka zan kira,nace sunanka zan kira? Spark yace yi hakuri,karka sake bani hakuri bana so...sannu to....a haka suka je asibiti,already ya kira Mima,tazo ita da Chika da Ikhy,Naila ana labour room ana fama. Nurse tazo da iyayi tana cewa ai da sauran lokaci ma akwai gumurzu a gaba,Naila ta yanka mata Mari ta shake ta tana cewa duk wannan azabar da nake Sha kice ba yanzu ba inji ubanki,aka kwaci nurse da kyar,gata yarinya Yar budurwa wata Yar mummuna me dama dama,Nurse dafe da kumatu tace wlh sai na rama Allah ya kaimu ki haihu lafiya,wlh sai na rama,Naila tuni ma bata San tayi ba,Mima tace kiyi hakuri kece yarinya ce baki San ba a zuwa Jikin me nakuda a daga mata hankali ba,nakuda hauka ce Inji nurse ta fice wajen Spark dake waje Yana kaiwa da kawowa,tace Kaine mijinta ko wlh idan matarka ta haihu sai na rama marina da tayi,kawai daga zuwa sai ta shake ni ta mare ni,nakuda hauka ce,wlh tana haihuwa sai na rama,Spark yace wuce ko na Kara miki uku kaga Yar iskar Kwaila in da nasan kece ma zaki je kan matata ki tsaya wlh bazan kawota wannan asibitin ba,so kike a haifo min yata ko Dana kamarki,in macece ki jawo min karbo mata rubutu domin ke sai kafin ki auru sai an karbo miki rubutu,nurse zata yi magana yace kina magana zanyi ball Dake a wajen Nan naga me tsaya miki,kin kalle min Bado Allah ya isa,idonki kadai ya isa yasa Badon ya rage zaki,kar wata nurse wata Yar iska me kambun Ido ta kallar min tsaraicin matata ta cuceni,duk gyaran duniya yaki dawowa dai dai,Nurse dai taji Spark ya fita iskanci Dan tijara ne tayi gaba tana jira Naila ta haihu tazo ta mareta. Spark dakin ya leka ta window yace Mima karanta mata falaki da Nasi da suratul Iklass kafa uku uku,Mima ta zaci na neman saukin nakuda ne ta fara tana tofa mata a ciki yace ba a nan ba ta Inda zata haihu ta Saman riga ba cewa nayi ki daga mata riga ba,nidai naga ta kaina me yasa ma ba a kira Goggo ba,ace sirika Taga wajen Danta ni ban yarda da wannan tsarin ba,Maman Rafeeq yaje ya dakko tun daga gida ya kawota,gashi asibitin mace daya ce zata shiga wajen marar lafiya,haka yasa Mima ta fito Maman Rafeeq ta shiga,ya sake lekawa yace bakinki kanin kafar ki kar naji kar na gani kin Fadi wani Abu akan palace dina,Maman Rafeeq tace kaima haka kake Ashe irin Arham ne mudai mun shiga uku da jarabar yara. Sai da ya kira Goggo a waya yace ta taho kawai,Goggo dama Jira take ana kauye an hadawa Naila kayan gyara in ta haihu za a taho Abuja a kula da ita,yace ki zauna yanzu zan sa Azo a taho dake,Shaheed ya biyawa flight Dana Goggo yaje ta Kano yafi kusa sannan ya hau mota drop har kauyen ya dakko Goggo da kayanta suka dawo ta airport suka shiga jirgi Dan lokaci kankani sai gasu a Abuja,Goggo kayanta ta ajiye a gidan Naila sannan Shaheed ya taho da ita asibitin,tana zuwa Spark yace Maman Rafeeq fito wata kusan tafi wata kusan,Kakar ta tazo da kanta ba sako ba,Maman Rafeeq ta tabe baki tace na huta,dama halinku ya isheni,ta fito Goggo suka gaggaisa da su Mima tace Allah ya raba lafiya ta shiga ciki. Mima suna zaune suna hararar Spark wai ya musu rashin kunya,su Chika suna ta yiwa Naila addua sunyi jugum jugum,Spark sai yanzu yasan ya tambaya yaji haihuwa da wahala,ya Kalli Chika yace wai da wahala ne haka,Chika tace la'ilahaillahu ai mutuwa ce da kanta,Ikhy tace azaba kenan bana marmari yanzu tuni muka yi planning bamu sakewa da wuri Inshaallah,Spark ya sake rudewa ko Sallah ya kasa yi sai da kyar,har dare shuru har yayi Sallar Isha shuru Yana ta addua, Ma'aikatan lafiya suna ta Bada agaji sosai,Naila aka ce tayi Nishi tace karfina ya kare bazan iya ba wlh,Goggo tace in zaki yi kiyi,Naila tace mutuwa zanyi,Spark zama yayi a kujera Dan kafarsa baza ta iya daukansa ba,sai ya fara hawaye tun Yana Yar kwallarsa a boye har ya kasa boyewa,ba sauti sai hawaye,Mima tazo tana lallashinsa tace zata haihu lafiya inshaallah ka daina damuwa duk haka muka yi muma,Spark yace wlh da nasan haka ne da banyi cikin nan ba,gwara ma kar nayi komai to kaddara da rabon za ayi haka,sai da ya basu dariya gaba daya har mutanen wajen da suke jinsu. Can yaji Naila tana wani irin Nishi tana gurnani kamar zata mutu,sai Kuma yaji kukan jariri ko murna baiyi ba shi dai Yaya Naila,Naila tana haihuwa ta daina gani sai a hankali ta farfado a hankali ta dawo hayyacinta,ta haihu lafiya komai ta gama shi lokaci guda babu wani jiran komai,Namiji ta haifo katon gaske sai yayi kama biyu shi ba Naila ba shi ba Spark ba haka yake,Spark yaji dai Muryar Naila tana cewa Goggo Alhmdllh nuna min shi,Ashe zan iya haihuwa,sai lokacin Spark yaji salama,Dan windon da yake lekawa sun rufe abinsu tuni sabo da ya dame su da leke tun farkon kawota. Mima suna Murna suka ce Alhmdllh da lafiya ma Inshaallah,Sai da aka yiwa Naila duk abinda ya dace da Allurai da komai suka cire mata Jinin mararta,ga Allura taji karfi a jikinta Goggo ta sa tayi wanka a toilet din,Dake asibitin na manya ne kamar kana gidanka ko Ina kamshi,haka tayi wanka da sabulu me kamshi tace kayan da suka baci a zubar,Goggo tace baki isa ba tana fitowa aka canja mata daki bayan Goggo ta wanke kayan da suka Baci,babu ma abinda ta bata sai iya rigar jikinta,Naila ta shirya kanta tace da kyar nake Shirin Nan iska daukana take sai naji bani da nauyi,Goggo tace ai kin samu me sauki wlh kin haihu lafiya wata ai bata Isa ta iya tashi yanzu ba,Naila tace Chika sai da ta kwana ma sannan ta iya yin wanka. Jariri Yana nade a cikin showel fari aka sa masa kayansa farare tas da shi Yana ta baccinsa. Spark ya matsu yaga Nailansa amma Goggo ta hana shiga sai sun shirya. Naila tunda ta canja kaya ta zura Abaya da wondonta dogo bayan ta shirya kanta ta kwanta bacci na son yin gaba da ita ga wahalar haihuwa,daga haihuwa ai baka isa kaji dai dai ba. Goggo ce tace ta fito daga wani dakin ta kofar baya ashe aka canja musu room,ta tako da Dan Nisa tace muna Nan fa kuzo kuga jariri da Me jego an haihu lafiya anyi arziki,Spark ne a gaba ya wuce Goggo tace har tayi wanka fa yanzu abinci nake so taci kafin ta huta,Spark yace yanzu za a kawo ai,suna shiga ciki suka hada Ido da Naila Dake kwance,suka sakarwa juna murmushi harda wani signa da Ido wai su sunyi Da,Mima ta karbi jariri tana cewa Masha Allah lallai an samu Karuwa,Naila tace Allah ya nufa,Goggo ta make ta tace ku ko kunyar Dan fari bakya ji a gaban sirika,Maman Rafeeq tace Allah ya raya bisa sunna,Naila tace Goggo nace Ameen?nidai zance Ameen ai addua ce,dariya aka yi Spark yace Allahumma Ameen,Spark ya Kalli Naila duk har ta canja da Gani ta Sha wahala,hannu ya mika mata Yana zaune a gefen bed din ta saka nata ciki,yace sannu kin Sha wahala,Finally dai an haihu na huta da cizo da kuka da masifa,Naila tayi dariya tace kunya ma nake ji yanzu in na tuna,yanzu me kike so? Cikinta ta nuna Masa tace yunwa kamar zanyi me a bani abinci Dan Allah,Arham ne ya shugo tare da Basma da flask wurin kala hudu na abinci daban daban,ga take away Kuma da Spark yace ya taho da shi na fruits da nama me ruwa ruwa, yogurt da sauransu,shayi aka hada mata lafiyayye ta mike zaune Spark Yana Bata a Baki sauran suna ta hirar su,Maman Rafeeq ta Kalli Arham taga ya juya can wai gyara mata adon rigarta yake bayan adon a Saman Boobs dinta suke,rankwashi ta zuba Masa tace Kai dai Allah wadaran halinka,nifa Mima gaba daya yaron nan naki ya kwance min Dan iska fitsararre,Arham yayi dariya yace idan kishi kike yi kawo na gyara miki kema gashi Nan an miki tuta a wajen ai,yaron ya karba Yana Masa addua,Maman Rafeeq tace Allah yasa adduarka tayi Masa aiki badalallen yaro,Mima tayi dariya tace kin da damar min yaro Dan kinje gidansa ya Koro ki sai ki dame shi,Arham yace gani tayi ana soyayyar da ita a zamaninsu babu irinta shine take kishi,Maman Rafeeq tace kaji min yaro ni da mijina yake Dan Sudan mene bai sani ba,har ka fadawa Balarabe kauna. Naila tana shanye shayi da nama kadan ta rage Naman,ta koma kan faten doya da wake taci taci ta koshi ta Sha fruits da ruwa ta Dan huta sannan ta kwanta sai bacci,tun dare sai washe gari da rana ma aka sallame su,Mima a motarta ta wuce da Naila da Goggon gidanta direct,Naila tasan Spark Bai sani ba ta dai yi shuru,sai da yaje gida shi yaga ba nan aka kawota ba,ya nufi gidan Mima Yana cewa ai dalilin dakko Goggo kenan tazo ta zauna da Naila. Mima tace to ai na sani Malam ka bari dai ta huta ,yace shi wlh a'a,Goggo tace ka bari tayi wanka sosai ta gasa jikinta ayiwa Jaririn sai mu tafi,yace yawwa,Spark tunda ya dauki Jaririn ya Masa addua bai Kuma daukansa ba Yana hannun Yan uwa har so yake a ajiye shi ya dauki abinsa amma daga hannun wannan sai ya fada hannun wannan. Nurse me jiran Naila ta haihu ta rama Marinta lokacin tashinta yayi amma jira take taki tafiya sai Naila ta haihu,tana can ta kwanta tayi bacci sai da me asibitin yazo ya dinga fada Dan me Bata tafi ba ya Kore ta gida,tace wlh Allah ya hada mu watarana a hanya ai na gane ta. Naila wanka tayi Goggo ce da kanta tayi mata gashi,Naila har hawaye tayi ta Sha wahala a hannun Goggo da gashin towel,an zuba gishiri a ruwan sabo da kashe wasu kwayoyin cutar,Sai da ta gama Naila tasa shampoo ta wanke gashinta sosai sai kamshi ke tashi,tayi wanka da sabulu ta fito,Mima tayiwa Jariri wanka tas an canja Masa kaya,kayan Naila na asibiti duk da Goggo ta wanke Spark gaba daya ya kwashe ya zuba a washing machine ya sake wanke su,ya zuba na jariri ma ya wanke tas suna kamshi ya tattara a cikin bahon jariri ko kunya,ya saka a mota yazo duk ya kwashe abinda suka zo da shi kaf ya Kai motarsa,Naila ta saka kaya tana daure gashinta da ribbon gashinta yanzu yayi mugun tsayi Dake Jinin gashi ce har ya dawo bayan uwar daadaa da yasha a gidan yari. Mima wani abincin ta shirya musu suka tafi da shi a mota tace ala raka taki gona ta fadawa Spark yayi dariya yace Ameen,zasu shiga mota Papa yazo ya dawo yazo ya dauki jariri ya Masa addua ya yiwa Naila murna,Spark yace sai fa kazo har gida Papa ban karbi wannan ba,Misam da Rafeeq har gida kaje ganin jariri Nima sai kazo,Papa yayi dariya yace zanzo Inshaallah,na Arham dai in za a haihu har asibiti zanje,dariya suka yi har Arham Dake ya fito shi da Basma zasu tafi,shi yasa Papa yayi zancen ma,Arham yace Allah ya kaimu,ai Bata da ciki wata nawa Amarcina nake Sha kawai ai haka yafi,Papa yace Allah ya bada na gari,yace Ameen yaushe zaka zo muyi hira ne?Papa yace sabo da yana son yayi hira da Spark da Arham,in suka zo ko banza yayi dariya,Rafeeq shi in yaga dama ma yaji yake ya daina zuwa,Misam ma basu Shaku ba,in yazo ma basa hira, Arham yayi dariya yace yau ma dan na gaji ne amma da tuni na zance ka da magana sai na dawo zanzo weekend ai Papa Soja sarkin fara'a,irin wai yasan baya fara'a sosai shine yace sarkin fara'a,Basma tace Papa mun tafi yanzu munyi hankali,Yace to Basma Haka ake so ayi ta hankali,tace to suka tafi, Papa yace a ransa Ina kuka ga wani hankali ai sai dai gaba kuyi hankali tare. Naila tun a mota ta kira Yan uwa ta fada musu,Mohsin ta fara fadawa,ta fadawa Umma ,ta kira wayar Abba sai da yaji ance ta haihu ya daga wayar Yana murna,tace Abba na haihu,yace Inyee su Naila an girma za a fara koya tarbiyya,Allah ya raya bisa sunna tace Ameen,yace yawwa karki biyewa su Goggo da kauyenci baza a amsa addua ba, kowa yace Allah ya raya kice Ameen, kanki tsaye ki amsa Ameen idan ance kinyi fitsara kice ni na saki kakan yaro ne,Naila tace Nima dai shine na Gani,yace yawwa karki yarda da kauyencin su Goggo,Sannan karki matsawa mijinki da maganar kashe kudi akan kin haihu nasan ku mata in kuka samu waje sai Kun Kai mutum bango ki bari duk abinda ya siya kiyi godiya,Naila tace ai dama Abba ai ba kullum ake kwana a gado ba,Abba da sauri yace a'a Banda ni" Naila kullum a gado nake kwana tun Ina jariri akan gado karami na babata ake dorani" babata Kuma da Mijinta babana kenan suna kan babban gado ni Ina karamin gado,har na girma aka mayar min da gadona dakina gashi har na auri Yar Inna yau shekaru kusan arba'in ban taba fashin kwana akan gado ba,Naila tace gaskiya ne tana murmushi,yace sai bayan suna zamu zo da Yar Inna,su Hidaya dai da su Zarah zasu zo kafin suna,tace to Allah ya kaimu. Suna komawa gida Naila tace yunwa nake ji da bacci,Spark wanka ya shiga yayi wanka sosai ya fito tare da saka sabuwar jallabiyarsa da Mohsin ya kawo Masa,Naila a dakinta Goggo ta sake yi mata wankan yamma,bata shirya ba sai da taci abinci dare yayi sannan kaya ta sake canjawa ta saka rigar baccinta doguwa me kyau me gajeren hannu Orange color, Goggo tace sai an daure ciki,Naila tasa abin daure ciki na Yan gayu Wanda a kasar waje ma aka siyo mata kala nawa da kyar ake matse ciki da shi na rage girman ciki,sai da ta saka sannan ta shafa turaruka ta Maida rigar Baccin kamar ba ta sa komai ba ciki ya lafe ya dame. Goggo ma wanka tayi ta fito ta hau Naila da fada yanzu dama da nace ki bashi nono Baki bashi ba? tunda aka haife shi sau daya kika bashi nono sai zam zam kawai aka bashi fa,wannan wacce mugunta ce,boyon nono ya kare yarinya cewar Goggo,Naila ta dauki Jaririn Yana ta cin hannu Yana zare Ido, Goggo tace tsaya na koya miki yanda ake yi,sai da ta koyawa Naila sannan tace to kiyi Bismillah,Naila tayi Bismillah ta juya baya ta fara bashi wai Goggo baza ta kallar mata nono ba,Goggo tace a gaban mu fa kika yi nono har ya girma me zaki boye min shashasha,naga dazu ni nayi miki wanka,Naila tace naji ga Abinci nan Goggo ki ebi abinda kike so,Goggo tace mijin naki fa? Na zuba Masa nasa kina wanka na Kai Masa,Goggo tace Iyye kaji kula da miji,dariya Naila tayi,Naila bayan ya Sha daya ta juya shi yanda Goggo tace ta bashi dayan,Yana Sha Goggo tace ai ya koshi haka,to rike shi a hankali karki hantsila shi zai yi amai,Naila tace Kai wannan yaro haba ace wannan ace waccen,sai da ya huta tace bari na kaiwa Daddyn sa shi ya ganshi,Goggo tace kwaji da shi munafukan banza wlh ki dawo a nan zaki kwana,Naila tace to,ta fice da danta cikin showel ta shiga dakin Spark Yana cin abinci Yana kallo ta shigo Ya kalleta Yana Jin dadi a ransa yace fada ya kare tace ae mana,kallonta ya sake yi yace wai dama idan an haihu kyau ake yi ne? duk naga in kuka haihu sai mace tayi wani kyau fatarta tana shining,Naila tace ai haka yawanci ake yi sai zuwa arba'in ake dawowa normal,Naila ta juyo fuskar jariri tace ka ganshi fa Kaine babansa Kai ka haifi wannan,Spark yace duniya sabuwa SparkNaila kamanninsa biyu,Naila tace Nima haka nace kamanninsa biyu,sai da ya gama cin abincinsa ya dauke shi,wanne suna za a sa Masa ne? Naila tace oho ka zaba,Spark yace Papa Ahmad in yayi miki a saka idan kina da zabi ki zaba,tace a'a Banda da zabi Kuma ai suna me dadi ne na kololuwa Ahmad fa,Allah ka raya Ahmad bisa sunna,Allah kayi Masa Albarka kasa ya zama mahaddacin Alqur'ani,Allah kasa yayi koyi da fiyayyen halitta Annabi Muhammad (SAW),Allah kasa duniya ta amfane shi,muma iyayensa ya amfane mu ya zame mana Alkhairi dukkanmu da Yan uwa da Al'ummar musulmai Baki daya,Allah yasa yayi suna ta hanya me kyau,ya shahara a duniya ta hanya me kyau,ba shaharar Dan Boko Haram ba,Bata Dan kidnapping ba,Bata Dan daba ko wani Dan iska ba,shahara ta hanyar abin Alkhairi,Allah yasa Shahidi ne,Allah ya Masa Albarka,Wannan Dan nawa Ahmad Allah ya sa Masa Albarka,Allah ya bashi lafiya da tsawon rai,Allah ya azurta shi ya raba shi da talauci,Allah yasa Dan Aljanna ne,Allah ya bashi mata ta gari Irina kyakyawa,Spark Yana ta amsawa da Ameen Ameen Yana dariya yanda Naila ta dage take surfa addua ta daga yaro sama tana cewa Allah ga Dana Ahmad,Allah ga Dana Ahmad,ya Rab ya Rab,ya Rab ka amsa addua ta. Tana gamawa Spark yace well-done uwa ta gari haka ake so wlh uwa ta fara yiwa danta,Shima ya karba yace kawo shi Nima nayi nawa Shima ya tallafe jariri ya Dan daga sama kadan ya fara zubo addua tana amsawa Ameen...Ameen..Ameen sai da suka gama sannan Spark yace yaushe zan dauke shi ne ya tsula min fitsari? Dariya Naila tayi,yace to ai ya kamata ace Danka ya Maka fitsari,Naila tace saurin me kake yi zaiyi ne ai bari a fara barin duwawunsa Yana hutawa ka gani,har Kashi ma zai Maka watarana,yace Ina maraba indai na dana nane,spark da baya daukan yaro amma shi yake neman fitsarin dansa yanzu. Naila ta dauki Baby tace bari naje sai da safe,sai da safe Ina?wai Ina bed din Baby ne,Goggo tace tare zamu na kwana,yace muje wajen Goggon ni zan mata bayani akan mene haka zamanin da ne wannan. Spark tashi yayi suka tafi da Naila yayi yayi akan Goggo ta fahimta amma Goggo taki yarda,fita yayi Dan yaji haushi,Naila tace Kinga yaji haushi in haka ne mene amfanin yace bazan zauna a wajen Mima ba,wlh ba wani Abu zai min ba,kin sani kema ba halin yin komai,sabo da haka yasa aka taho dake,kullum muna tare dake da jaririn ace bazan kwana a can ba,Goggo tace wlh bari na kira uwarki na fada mata tunda baki da kunya tafiya zanyi,Naila ta kwanta a gadon ta ajiye Baby a gefenta,Spark shi kadai ya kwana ya hakura Kuma da safe ma bai ce komai ba bai nuna fushi ba ko a fuska har wasa suka yi da Goggo,washe gari haka Goggo tayi komai na gidan ta gyara ko Ina ta kula da Naila da Baby,girki me aiki tayi,haka Naila ta sake kwana da Baby da Goggo har kwana uku,kwana na ukun ta kira Abba a boye ta fada Masa,Abba yace kyaleta bari na kira ta mu zata zowa da kauyenci garin Abuja,Abba ya kira Goggo ta daga waya,yace wanne dalilin zaki je ki Hana su sakewa daga ganin sarkin fawa sai Miya tayi zaki,birni ba haka ake yi ba yanzu,ki kyale yarinya,Goggo tace so take ayi mata wani cikin da wuri,ayi mata mana ke Ina ruwanki a jikinki yake,ana ta murna a kira Goggo sai kizo ki watsawa mijinta, kisa musu Ido ki kyaleta,iya aikinki kiyi Dan Allah. Goggo tace shike nan tunda ku birni Kun lalace babu kunya taje ta kwana,idan yaro Yana kuka ai tayi sintiri a hanya zuwa dakina, yace ba komai tayi sintirin ai Matashiya ce da Kwarin ta kafafun basu fara ciwo ba ya kashe wayarsa. Naila tana shugowa Goggo tace munafuka har da fadawa ubanki kije kiyi ta kwana ai mayyar miji,dariya Naila tayi tace naji. Yau da dare bayan Yan barka sun tafi tayi wankanta ta saka riga da wando blue na bacci ta Sha kyau ta dauki Danta ta yiwa Goggo sai da safe,Goggo ta tabe baki,ta shiga bedroom din Spark,baiyi tunanin kwana zata yi ba,yace Goggo ta ishe ni da nasan haka ne bazan kawo ta ba wlh,Naila ta fara hada gadon Baby a gefen nasu hadadden bed fari tas da shi,Spark yace ta yarda ne ki kwana? Naila tace tun yaushe na fadawa Abba ya kira ta a waya kuwa yace ba ruwanta da mu,Spark yaji dadi yace yawwa tsohuwa ta ishe ni haba,Naila tayi dariya ya dauki Baby,yace yaron nan ya bani wahala kafin yazo duniya,Naila ta bashi nono ya Sha ta kwantar da shi. Yayin da Maryam kanwar Annoor ta samu miji bayan ta murmure tayi aure abinta itama,suna ta zumuncinsu da Annoor. Ihsan tana yin Idda ta samu saurayinta da take so tace tana sonsa bayan ta bashi jari ya kama business babba,ta kashe Masa mugun kudi,ta siya Masa mota bai taba cewa Yana sonta ba sai dai ya nuna shi kawai birge shi take yi,tun tana jira yace Yana sonta har ta gaji ta fada Masa da kanta,kowa ya gansu zai ce masoya ne yanda suke mu'amula,suke waya,yake zuwa gidanta da sauran su,yaci kudinta matuka,Ashe shi Yana kama kasa ya koma wajen Tsohuwar budurwarsa da aka hanashi sabo da baida sana'a Yana komawa aka ce ya turo Kuma ya Kai kudin aure,a ransa yayi tunanin ko ya auri Ihsan din sai yaga tafi karfinsa ita tana da kudi baza ta juyu a wajensa ba kawai ya nemi dai dai shi,sai da Ihsan tace tana sonsa yace ai shi an saka ranarsa da wata,Ihsan ga aji tace ba komai ba damuwa kamar gaske ta nuna bata damu ba, Ashe Kara ta shigar kotu ta kashe Masa kudinta ya yaudare ta zai auri wata. Sai da suka je kotu sannan ma yaji labari ta taba aure duk lokacin da take kulashi tana da aure,Nan yayiwa Allah godiya da bai aure ta ba, Alkali yaji ma kudin ba roka yayi ba babu manufa kawai ta dinga kashe Masa kudi,Alkali yace ficika bazai biyaki ba tunda ba yarjejeniya kuka yi ba,haka kawai kika bashi kyauta Kuma kin amsa da kanki kyauta kika bashi,Ihsan tace Dan me bazai gane sonsa nake ba shi Dabba ne,Sadeeq me kurkura yace nasan gaibu ne ni da zan gane abinda ke ranki,Alkhali ya dakatar da su yace Allah ya azurta Sadeeq ta hanyarki,ki hakura ki nemi ladan Allah sai Allah ya baki wani na gari,Ihsan tace ni ban yarda ba,Alkali ya Kori Kara yayi rubutu matukar ta takurawa me kurkura sai an yanke mata hukunci,Ihsan ba nasara ta rasa Inda zata sa kanta gashi ta bari an sake ta,gidanta na Kano ta dawo ta kwana tana kuka da dana sani,washe gari da safe ta nufi gidan Haneef. Gidan ta gani komai ya canja ya Kara haduwa,sababbin motoci ba Wanda ta sani ba,ta danna door bell,ba a Dade ba Khadija ta bude kofar wow,ta zama wata Yar gayu da ita,ta Kara kiba da haske ta zuba kyau cikin kana Nan kaya,Ihsan mamaki ya kamata kamar ba Khadija ba,fuska ta bata tace uban me kike a gidan nan har yanzu,Khadija tace ubanki nake yi,an sake ki me ya kawo ki nan gantalalliya,Khadija ta kalla sosai taga ciki a jikinta bakin ciki ya tokare Ihsan a makoshi,Honey Mero ta shiga kwalawa kira ya fito yana cewa na'am Beb,yaga Ihsan da mamaki yace ke me ya kawo ki ya bata rai,Ihsan tace Baby Dan Allah kayi hakuri,Babyn ubanki dalla fitar min a gida,rungume Haneef zata yi Khadija ta fyalle mata Mari, tace dama haushinki nake ji an sakeki ban sani ba,Haneef yace fitar min a gidana Ihsan,ni kake kora Haneef Ina Yar uwarka yace an Kore ki,karki zubarwa da matata ciki da fadan masifarki,ya fisgi Hannun Ihsan ya bude kofa tare da jefata waje ya kulle kofarsa,Mero harda goge masa hannu kamar ya taba Kashi ta goge masa tace muje. Haneef ya dakkowa Mero me koya mata karatun Boko tana yi sosai sannan zata zana waec Nan gaba ya sata a makaranta,gashi ya siyawa Jummai gida madaidaici a birni tare da danta Mummir,ya saka Munnir a makaranta sannan ya bude Musu katon shagon cosmetics,Munnir Yana juyawa,Jummai tana siyar da kayan kanti shago guda ya mata a gidan,abinci da komai basu rasa ba,sannan da su za ayi aikin hajji badi harda Mero da shi zasu tafi gaba dayan su. Mero tace ya kamata naje har gida na gaida Spark da su Mima suga ci gabana,sannan naje prison na nunawa Mummy da tace ban dace da suna Khadija ba sai dai Mero,Ina ji ina Gani ta rada min Mero,sabo da banyi Ilimin Boko ba bamu da kudi mu Yan kauye ne,gashi yau ita ta kare mata ni Kuma Allah ya daga ni,Haneef yace ya kamata kuwa muje gaskiya,Mero tace girki zan mata me dadi na Kai mata prison taci arzikina mutuniyar banza Tsohuwar alakwankwan,Haneef yayi dariya yace kaji za a Kai mata farfesu ma,Mero tace farfesun kaji Maja zan mata. AsmaBaffa [3/10, 12:13 PM] AsmaBaffa: 🏫TANTIRIYA🏫 A GIDAN YARI BOOK 3 ~TAIMAKO~ 91-100 Official By AsmaBaffa SADAUKARWA NE GA AIDA MAMAN TASNIM PAGE NAKU NE. Oufadi Raliyaisah615 Spark ya kashe kudi na kirki Naila kaya masu tsada kamar me hada lefe haka ya mata su gaba daya ta zabe kayanta wasu duk ta cire kwance da marasa karfi Dake kusa da gidan Abba,da wasu na kauye gaba daya ma duk ta ware musu za a tafi musu da shi,ga gift kala kala tun kafin suna ana ta kawo mata,ko Kamal kayan da ya kawo na jariri ba a magana, saura kwana biyu suna Hidaya,Iman,Mufee,Beauty,Zarah da Aslam duk suka zo sai su Tani daga kauye,Spark ya kama musu Event center suje can suyi taron suna ba a gida ba,har anko su Chika suka yi. Naila anje gyaran gashi saloon an Sha uban lalle me kyau kamar Amarya,haka su Ikhy ma. duk sun gama shirya komai abinsu sai 12am ta shugo bedroom din Spark tayi wanka tayi Shirin bacci,yace ki kwashe kayan Nan na jariri da naki sun cike min bed,tace na gaji Allah ta fara kwashewa ya tayata suka Adana ta canja sabon bedsheet ta gyara bed din sannan ya Sha shayin na'a na'a ya kwanta tana gama shafa turaruka masu kamshi na musamman,Spark Yana kallonta sai kace maye,Juyowa tayi taga ita yake kallo,dariya ya bata ta murmusa yace nifa kyawun naki sai mamaki yake Kara bani zo mu kwanta,light ta kashe musu Baby Yana ta baccinsa a bed,Spark ya shigar da ita jikinsa,yace Hallare agaji take nema a taimaka mata ko da mouth ne,Bata Masa musu ba haka ta murje mijinta tass ta jiyar da shi dadi ba tare da anyi wani sex ba ta gamsar da shi. Washe gari suna ba Wanda yazo gidan Naila a masallaci aka radawa yaro Ahmad,Papa yace kawai a dinga ce Masa Muhammad kar a canja Masa wani suna tunda shi da Ahmad aka sanshi,amma duk da haka iyayin Naila harda cewa tunda ga Spark ai ya kamata ta samu Flash sabo da haka ita Flash tayi masa nickname dinta. Da safen kaya iri daya suka saka da Spark wata dakakkiyar shadda wata baka,Dake farare ne sai suka zuba kyau ciki,Ahmad ya Sha kayansa Yan kanti wasu farare tas. Su Rafeeq ne suka zo wai sunzo cin tuwon suna,Spark yace sai dai ku Sha tea,Zarah ce ta fito da jaririn,Arham yace ko dai wannan ni take jira na Kara ta biyu ne itama na Dan ji,Shaheed yace da kuwa Kaci ubanka wannan matar taka,Rafeeq yace ka kyale shi ba iyawa zaiyi ba Kaine ma kayi Masa magana. Naila ce ta fito da jariri ta Sha takalmi da jaka farare,Spark ya mike yace sai pics,Kamal ya gyara Iphone dinsa ya dinga daukansu romantic pics ga Baby a tsakiya sannan suka yi da sauran suma su Arham,aka dinga pics harda su Goggo da su Zarah. Zuwa yamma Naila ta Sha Bride material me shegen kyau da tsada,gown dinta ta Sha dinki sosai matuka tana wajen make up su Chika ma sun zuba anko duk sunje make up, Spark zuwa yayi ya dauki Naila da kansa driver ya kawo shi ya Sha shadda silver kalar takalmi da Jakar Naila,ta zuba kyau kowa ya zaci Amarya da Ango ne suke aure abin nasu yayi,Mota suka shiga sai Event center,mata da Maza har Yan school din su Naila,suna zuwa can Basma ta fito daga motar Arham jariri Yana kuka ta kawowa Naila mota,a motar Spark yace da driver Dan Allah Dan bamu waje,Driver ya fice sannan Naila ta bashi nono ya Sha,Tana gama bashi nono aka musu pics sannan suka shiga,mutane an hallara su Mima,yaro ya Sha kaya masu kyau white and silver,duk kidan Dake tashi baccinsa Jaririn yayi,kowa yaci abinda yake so anyi rawa an zubar da Naira sosai,su Chika an cashe da Beauty da Ikhy... Kamal da Amaryarsa ma sunje,ana cikin riti Mero da Haneef suka dira a Abuja amma suna hotel masauki,Mero harda cewa an kawo motar taka kuwa? Haneef yace an kawo Madam driver Yana nan zai kaimu Inda kike so,tace to Allah ya kaimu. Washe gari da Yamma suka shirya Mero an goge ta Sha kaya masu tsada Leshi kana gani kasan kayan ba karya a ciki dark green an Golden ne. Mota suka shiga driver ya kaisu har gidan Mima,Allah yasa duk sunzo Sunan Naila basu tafi ba kowa da kowa Yana gidan Mima,da yamma su Misam,Rafeeq,Arham da matayensu duk suna gidan,suna compound sai kace yau ake Sunan,Badia tazo da Anam,motar Haneef me azabar tsada ce ta shugo gidan sun zaci ma Spark ne,Sai da Mero ta fara fitowa tun daga takalminta da komai na jikinta abin a kalla ne,ba Wanda ya ganeta har takaraso gabansu tayi Sallama suka amsa,tace Mima sai lokacin Maman Rafeeq tace wace haka kamar Mero Yar aikin Maman Spark,Mero tace nice tana murmushi,Mima tace Mero kece haka ai badan kinyi magana ba babu me gane ki,suka hau mamaki,kowa sai da ya kalle ta,tace dama da mijina muke munzo Abuja ne nace bari muzo mu gaisa,Mima tace to ya fito mana ku shugo ciki sannunku da zuwa,oh Ashe kinyi aure ba sanarwa,Mero tace abin ne ba shiri shi yasa. Arham harda gulma kasa kasa ta furta Mero Yar aikin Mama mutuniyar Spark,Rafeeq yace ni naga dare Daya Allah kan yi bature yau,shi yasa aka ce ko ya mutum yake baka San me Allah zaiyi ba karka wulakanta shi amma su Mama basa ji,Arham yace ei kamar Mamanka wulakantani da take akan Ina soyayya Baki San me Allah yayi ba wlh Kinga dai Mero,dariya Maman Rafeeq tayi tace Dan banza ai Kai sai gyaran Allah. Haneef ne ya fito ya Sha gezna Yar gasken milk sai shining yake,Sai sa Ido suke yi yaran Mima,mazan ya mikawa Hannu suka gaisa matan Kuma suka gaida shi suka shiga ciki,Anam tace guy din ya hadu ita Mero Dan ubanta Ina ta samo wannan haka ikon Allah kenan daga yau na daina wulakanta Yan aikina wlh naga ishara na tuba,Arham yace kuci gaba duniya ce ai zata bi da ku,ku akan Kuna yaran General sai iskanci,ai da kunce zaku wulakanta min Basma sawa zanyi ta zazzage ku,ki duba dai Maman Spark yau suna Ina,ga Wahida sarkin bakin jini anyi bikinta tana dakin mijinta uwar tana prison,yanzu Kalli Mero dai wannan Mero da ake gani a banza ana mata kallon mahaukaciya ce ma. Basu dade ba suka fito suka musu sallama suka bar su da Cece kuce,gidan Spark suka je,Naila ta gama gyara kayan gift da komai Baki duk sun tafi har su Zarah sun tafi sabo da makaranta,Naman Sunan ma tace sai dai gobe a Kai musu,masu aiki suna ta soya nama a can compound sabo da sa ne da raguna biyu kamar me layya,Naila tana Palo ita da Goggo Sai taji sallama ta amsa,Mero ce ta shugo,Naila ta ganeta ita" tace Mero kece? Mero tayi murmushi ta shugo tace nice ta durkusa ta gaida Goggo,ta zauna suka gaisa da Naila tace ke Yar gari Ashe haihuwa kika yi? Naila tayi dariya tace ae jiya aka yi suna Mima ce ta fada min da naje,Allah ka sa Nima na sauka lafiya haka,Allah ya raya,Naila tace kema naga kamar kina da cikin Ashe da gaske ne,wai yaushe kika yi auren ba sanarwa? Mero tace Abu ne yazo cikin gaggawa,wlh ujula ujula aka yi auren nan,tare muke da shi ma Yana mota,Naila tace kice ya shugo mana,Mero ta fita ta shugo da Haneef,Naila taga miji rangadeden gaske,bayan sun gaisa tace bari na kira muku shi Yana nan,sama ta haura Spark Yana aiki a system tace kazo munyi Baki Mero da Angonta sun zo,Mero tab aure tayi? Naila tace har da ciki,yace ikon Allah,Naila tace zo kaga Mero ta goge me hali ta aura,Spark yace na tayata murna,ya mike suka fito,ahhhh bai zaici gogewar Mero ta Kai haka ba,mijin ma ya sanshi ashe ya Sha ganinsa a gidan yari in yaje ziyara,suka gaisa Sosai ya zauna suna ta hira,Naila ta kawo musu Abinci da lemuka sannan ta kawo musu Naman da ake soyawa a plate,suka ci kuwa sun Dade kafin su tafi, Haneef 50k ya bawa Naila suka tafi har mota Naila da Spark suka raka su,Naila tace sai mun zo muku muma inshaallah,Mero tace Allah ya kawo ku. Wani satin Mero da Haneef sai prison wajen Maman Spark,tayi girki lafiyayye suka Kai,bayan Mama ta fito da Yar uwarta da kyar suka gane Mero,Mama ta nuna ta da yatsa tace me...me...Mero tace nice Mero da kika ce ban dace da suna Khadija ba sai dai Mero,to ga Mero Allah ya azurtata tayi sama ke Kuma gaki a wani hali,ni bazan miki abinda kika yi min ba,albarkacin naci na Sha a gidanki baki taba hanani abinci ba bazan manta da wannan Alkhairin ba,ko nama kika ci Ina ci,tace gashi ta mika mata Daya abinci da ta kawo mata,Maman Wahida ma suka gaisa suna ta mamakin ikon Allah,Azima ce tazo suka rungume da Mero sannan Mero ta bata nata abincin,Haneef harda kudi ya basu duka,sun Dan dauki lokaci sannan suka tafi,Mero tana cewa Azima ki gaida su Goje su Scola kice bazan manta da su ba,Azima tayi dariya tace zasu ji. Naila tana yin Arba'in Spark ya dauke ta da Baby da Arham da Basma suka bar kasar suka tafi Germany,Arham sai murna yake zasu Shana,Rafeeq yaji haushi an bar Masa aikin Office a hannunsa,Misam kuwa ya biyawa Mahaifiyar Chika da Mahaifinta Makkah,ya canja musu gida me kyau. Spark amarcinsa yake Sha kawai sai da suka kwashe watanni kamar baza su dawo ba suna zaga kasashe,suna dawowa Kuma Jauro ya biyawa Yar Inna da Abba Dolo Umrah da shi kansa Jauron da iyalansa kaf,suka tafi wai za ayi addua har su Haidar da matayen su. Lokacin aikin hajji ya kusa Iman ta haifo Yarta mace kyakyawa,ba a Dade ba Hidaya ta haifi Danta Namiji itama,an Sha suna anyi shagali,Yar gidan Iman Sunan Maman Annoor aka sa mata tana kiranta da Nihad,ita Kuma Hidaya suna kawai danta ya ci Na'eem. Naila da Spark,Rafeeq da Ikhy,Basma suka tafi sauke farali gaba daya Spark ne ya biya musu,Chika alkawari yayi zai biya mata dama,can suka hadu da su Abba Dolo,Abba Dolo da Yar Inna kamar Larabawa suna makale da juna. Bayan Sallah suka dawo Mero ta Haifo Yan biyu mace da namiji kyawawan gaske kamar yaran Larabawa,kowa sai murna ake taya su,Spark ma yaje da Naila da Sha Tara ta arziki yara sunansu Nawwar da Nawwara ,su Mima sun je,Mufee da matar Kamal ma da yaron cikinsu. Sai da Basma ta Shekara biyu sannan ta samu ciki,Arham ana ta murna da kamar baza ta haihu ba itama, lokacin su Chika ma yaransu sun fara tafiya dagwai dagwai,na Naila Yana Rarrafe ko Ina,ga matar Kamal ta haihu itama Rayuwa na ja kowanne suna zamansu lafiya sai sabani Wanda ya zama dole da sauran kaddarorin rayuwa domin bawa baya zama babu kaddara da jarabawar rayuwa,cikin Basma ya tsufa itama gida ya dauke ta suka koma gaban Mima,satinta biyu a gidan da tsakar rana ta fara nakuda Arham Yana wajen aiki,Mima Bata fada Masa har suka Kai Basma asibiti ta haifo yarta mace kyakyawa,duk ba a fadawa mutane ba sai yamma likis aka sallamo su,tazo ma tayi wanka aka yiwa jaririya wanka suka shirya tsaf ta gwada bashi nono,Arham sai wajen dare yazo gidan ganin matarsa yaya take,Mima ya gani yace Basma fa ya jikin nata? Mima tace tana daki shiga mana ka ganta,Yana shiga ya ganta da jariri a hannu tana cin Abinci,Arham yace wai haihuwa kika yi? tana dariya tace gashi ka gani kuma,ya dafe kirji yace wayyo dadi, Alhmdllh Alhmdllh,Mima tana jinsa Yana hauka iri iri,na zama Daddy wannan yarinyar zata ga muzurai ince ke shiga gida,dariya Basma tayi tace ni Kuma nace wato baza ki shirya ki tafi school din ba sai kin makara wannan yarinya Allah ya shirye ki bari na fadawa Daddy,sai na kwala ma kira Daddy Daddy,Arham harda kausasa Murya na'am lafiya,ka zo taki ta shiryawa ta tafi school,sai na fito na mata wani kallo tuni Zata kama gabanta,dariya suka yi sannan ya zauna ya dauke ta yace a'a Kai nayi 'ya kuma ni,Anya zan iya bacci ma,Basma tana ta dariya,Mima ta sanarwa dangi da kowa. Su Arham sunga jama'a kullum cika akeyi yayye da sauran dangi da abokan arziki,ranar suna yarinya taci Sunan Mima suna kiranta da little Mima,Mima an Maida sunanta sai farin ciki take yi sosai yarinya tana gani gata,Papa yace matarsa guda ai sai abinda take so a duniya. Azima kuwa ta Jikin katanga ta fadawa su Scola sakon Mero har yanda tayi kyau da Wanda ta aura,Goje yace mu dai mun shiga uku ko wacce muka Shaku da ita sai ta bar gidan yari ta auri me kudi daga yau baza mu sake kula ko wacce ba duk kuje Yan iska Shegu,'ya'yan mutanen banza ,kana shakuwa da mace sai kaji fit ta fice tayi aurenta,Dan Indo yace abin bakin cikin ma sai kaji Dan prison ne,yanzu dai ji Tantiriya da wannan Dan iskan Spark shege Dan giya,Scola suka sheke da dariya yace Spark dinne Dan giya? Da mene idan ba Dan giya ba Yana magana Yana lumshe Ido kamar zaiyi bacci in ba giya yake Sha ba ubansa Soja yake Sha? Marar neman Albarka,suna ta dariya Scola yace kaji ance ta haihu ma Naila,Dan Indo yace ta haihu? aka ce tsohon zance yace a gidan yari a Nan ya mata ciki,da abinta ta shiga gidansa,daga Dan auren har ta haihu a nan yayi mata ciki karya suke,scola suka dinga dariya da ihu,Dan Indo yace ana kallonta a namiji Ashe shi harka kawai yake Kwasa Allah wadaran Spark kaji, ban taba ganin Dan iskan yaro ba irinsa,suna ta dariya,Malam Jilani Yana zaune yace wallahi Haramun kake aikatawa ranar lahira wlh sai ka Bada shedar abinda ka fada an rubuta,Dan Indo yace Kai rufe mana baki munafukai duk ba da ku aka hada baki ba,Kun fake da karatu,kasan kana fadar gaskiya kazo ka fada mana macece tun farko mana,sai anyi magana ka makale Murya kamar zaka yi amai wai ke Balarabe munga Sudais da Shuriem ma karewa,gashi Nan sauran Yan uwanka malamai sun fita sun barka,su Malam Garzali Kai kana Nan sai ka Kara wata uku sabo da bakin hali,Malam Jilani yace Kai yaushe zaka fita? Kai da aka yanke Maka hukuncin daurin rai da rai,shuru suka yi Dan Indo Yana Jan Kwafa. Abba da Yar Innar sa suna zaman su lafiya,sana'arsa sai yaga dama ma yake yinta yau rana tana takewa ya gudo gida yayi kwanciyarsa,yaki fita sai Aslam ne ya zauna a shagon ya siyar, Yar Inna tace baza ka fita ba kenan? Yace bazan siyar ba na gaji Wanda ya dogara Dani ma a unguwa ya dogara da aikin banza,in zai kama me sana'ar arziki ya kama ya dinga siyen kayan masarufinsa a can,ni na gaji da auna hatsi nauyin tsiya,sai ka jawo buhu ga nauyi ka zuba a daro,wajen kamfatowar ma ba arziki sai nauyi duk kasusuwana sun fara budewa,sai damatsa nake ajiyewa sai kace Dan dambe,Yar Inna tayi dariya kamar me tace Ina kaga wasu damatsa,in ma kayi damatsa ai haka ake so,ke Yar Inna ki rage budurwar zuciya so kike Naila da Hidaya na auren masu damatsa kema kice irinsa kike so na koma,shi yasa wato naga kin yarda da sana'ar lokaci guda,Yar Inna tace Allah ya kiyaye Kai yanzu ko Gym kake zuwa Ina zaka tara damatsa,Abba ya kwanta ya mimmike yace wayyo Hashimu kwanta ka huta. Annoor da Iman dinsa suna joint na Shan Ice cream da shawarma,aka kawo musu suna zaune,Baby tana cinyarta ya shiga bawa Iman a Baki tana ci suna hirarsu ta masoya,Ice cream din yake bata tana Sha,sai wani ya fado fuskar yarsu har da rige rigen lashewa a fuskar yarinyar,ya riga Iman lashewa,hannun ta doke tana shagwaba tace ka min wayo Allah dariya yayi yace ni da 'yata kin tsaya kina yanga,wajen kida na tashi harda rawa da hanu Yana bata tana cin shawarma abinsu sharr. Nabeel tare da Hidaya suna gidan Haidar,Haidar dinma Yana Nan suna ta hira abin su a gidan suka yini. Su Nabeela ma sun haihu suna zaman su lafiya da mazajen su suna zumuncinsu. Mero tana Jikin mijinta a bedroom suna hutawa,tace wai Ina Yar uwarka Ihsan ne?yayi murmushi yace tana Nan Kano tana aikinta ta rasa mijin aure har yanzu,ita Kuma auren take so yanzu hankalinta ya dawo jikinta amma ta rasa mijin,taje Adamawa ta dade ta dade ko zata dace amma Ina,ta dawo Kano duk yawan Al'ummar Kano ta rasa mashinshini duk ta rame to karshe dai abokina Yana sonta yanzu zo Kiga murna zai Kara ta biyu da ita,Mero tace maganin marar hankali kenan duniya makaranta,shi yasa in mutum yace shi duniya ya sa a gaba to zai ga duniya,dariya suka yi yace Allah ya kyauta ya raba mu da aikin dana sani ya ja musu Bargo suka shike suka fara soyewa. Spark kuwa Naila tana samun hutu ya dauke ta suka bar kasar tare da Baby dinsu,suna jirgi suna daukan pics cike da nishadi,Baby Yana ta kiriniya gwanin sha'awa,Naila wata ta Gani a jirgi babbar mace tace Dan Allah dauke mu ta bata wayar matar ta dauke su pics da videos sunyi kyau,Naila tace Kalli yanda muka yi kyau ya Kalli pics din ya mata rada a matse nake Baby uwar Baby matar Baby ta Baby da Babynta Kuma gata Baby itama muna sauka a bani bado,dariya tayi tace Ina Jin wannan kirarin nasan me ake so dai, yayi dariya Yana tuna masifar Naila lokacin tana da ciki ya dinga dariya Yana tuna mata itama dariyar take,tace wlh in na tuna dariya nake yi,Kunnenta ya ciza kadan sannan yace Allah ya barmu tare,tace Ameen Baby Mijin Baby Baban Baby,dariya suka yace Ameen Ameen Allah yasa ko wata na Gani idan zanje zance nayi makuwa nayi batan kai na dawo gida wajenki,Naila ta sheke da dariya tare da furta Ameen. INA BAWA FANS DINA HAKURI BISA MATSALA DA AKA SAMU A WAJEN POSTING. WANNAN LITTAFIN NA SAMU MATSALAR TYPING WLH BAN YI SHI CIKIN DADI BA,SABO DA YAZO MIN A BANI DA LAFIYA,GA ZUWA ASIBITI LOKACIN DA AKA SHIGA BOOK2 HAR KUSAN FARKON BOOK3,A BOOK3 KUMA UZURI YA SHIGO MIN DA YAWA BA ZATO WANDA YA JAWO DELAY DA YAWA A LITTAFIN,BAN JI DADIN HAKAN BA SABO DA KOWA YA SABA BANA BOOK HAKA A DADE BA A GAMA BA SANNAN BANA FASHIN POSTING SAI DA DALILI ME KARFI,WANDA A WANNAN BOOK DIN HAR NA GAJI MA DA BADA UZURI,BANA FATA NA SAKE TYPING ME DELAY HAKA,NI KAINA BANA JIN DADI WLH AMMA DUK DA HAKA ALHMDLLH INA GODIYA GA ALLAH DA YA BANI IKON KAMMALA WANNAN LITTAFI LAFIYA DA NI DA MASOYA WANNAN LITTAFIN TANTIRIYA A GIDAN YARI. INA MIKA GODIYA TA GA DUKKAN WANDA SUKA SIYI LITTAFIN NAN MAZA DA MATA,SUKA SA KUDIN SU SUKA SIYA INA MATUKAR GODIYA ALLAH YA BIYA MUKU BUKATUNKU BAKI DAYA,ALLAH YA YANTA KU CIKIN YANTATTUN BAYINSA A WANNAN WATA MAI ALBARKA DA ZAMU SHIGA. CIKIN SAURI NA KARASA WANNAN LITTAFI KASANCEWAR AZUMI YAZO WATAN IBADA. WANDA SUKA JAJIRCE DA YI MIN SHARHI KO YAUSHE HAR MUKA GAMA NOVEL DIN NAN WLH BAN SAN MA DA BAKIN DA ZAN GODE MUKU BA MUSAMMAN BABY AK AMINA YUSUF BAWALE HAJJORA INVESTMENT MURJANATU ABU NA BANGA DA DAI SAURAN SU INA GODIYA. SANNAN WANDA SUKA JAJIRCE MA FARKO HAR AKA YI NISA UZURI YA SHUGO MUSU INA GODIYA,DA SAURAN WANDA BASU SHARHI BA KUMA INA KAUNAR KU NA GODE MATUKA. MASU JIRAN COMPLT KUMA DA KUKE GEFE NA GODE. ALLAH YASA MUYI IBADA KARBABBIYA. ALLAH YA BAMU LAFIYA ME DORARRIYA ME AMFANI BAKI DAYAN MU INA YIWA KOWA FATAN ALKHAIRI MASOYA. AsmaBaffa [3/10, 12:24 PM] AsmaBaffa: 🏫TANTIRIYA🏫 A GIDAN YARI BOOK 3 ~TAIMAKO~ 91-100 Official By AsmaBaffa SADAUKARWA NE GA AIDA MAMAN TASNIM PAGE NAKU NE. Oufadi Raliyaisah615 Spark ya kashe kudi na kirki Naila kaya masu tsada kamar me hada lefe haka ya mata su gaba daya ta zabe kayanta wasu duk ta cire kwance da marasa karfi Dake kusa da gidan Abba,da wasu na kauye gaba daya ma duk ta ware musu za a tafi musu da shi,ga gift kala kala tun kafin suna ana ta kawo mata,ko Kamal kayan da ya kawo na jariri ba a magana, saura kwana biyu suna Hidaya,Iman,Mufee,Beauty,Zarah da Aslam duk suka zo sai su Tani daga kauye,Spark ya kama musu Event center suje can suyi taron suna ba a gida ba,har anko su Chika suka yi. Naila anje gyaran gashi saloon an Sha uban lalle me kyau kamar Amarya,haka su Ikhy ma. duk sun gama shirya komai abinsu sai 12am ta shugo bedroom din Spark tayi wanka tayi Shirin bacci,yace ki kwashe kayan Nan na jariri da naki sun cike min bed,tace na gaji Allah ta fara kwashewa ya tayata suka Adana ta canja sabon bedsheet ta gyara bed din sannan ya Sha shayin na'a na'a ya kwanta tana gama shafa turaruka masu kamshi na musamman,Spark Yana kallonta sai kace maye,Juyowa tayi taga ita yake kallo,dariya ya bata ta murmusa yace nifa kyawun naki sai mamaki yake Kara bani zo mu kwanta,light ta kashe musu Baby Yana ta baccinsa a bed,Spark ya shigar da ita jikinsa,yace Hallare agaji take nema a taimaka mata ko da mouth ne,Bata Masa musu ba haka ta murje mijinta tass ta jiyar da shi dadi ba tare da anyi wani sex ba ta gamsar da shi. Washe gari suna ba Wanda yazo gidan Naila a masallaci aka radawa yaro Ahmad,Papa yace kawai a dinga ce Masa Muhammad kar a canja Masa wani suna tunda shi da Ahmad aka sanshi,amma duk da haka iyayin Naila harda cewa tunda ga Spark ai ya kamata ta samu Flash sabo da haka ita Flash tayi masa nickname dinta. Da safen kaya iri daya suka saka da Spark wata dakakkiyar shadda wata baka,Dake farare ne sai suka zuba kyau ciki,Ahmad ya Sha kayansa Yan kanti wasu farare tas. Su Rafeeq ne suka zo wai sunzo cin tuwon suna,Spark yace sai dai ku Sha tea,Zarah ce ta fito da jaririn,Arham yace ko dai wannan ni take jira na Kara ta biyu ne itama na Dan ji,Shaheed yace da kuwa Kaci ubanka wannan matar taka,Rafeeq yace ka kyale shi ba iyawa zaiyi ba Kaine ma kayi Masa magana. Naila ce ta fito da jariri ta Sha takalmi da jaka farare,Spark ya mike yace sai pics,Kamal ya gyara Iphone dinsa ya dinga daukansu romantic pics ga Baby a tsakiya sannan suka yi da sauran suma su Arham,aka dinga pics harda su Goggo da su Zarah. Zuwa yamma Naila ta Sha Bride material me shegen kyau da tsada,gown dinta ta Sha dinki sosai matuka tana wajen make up su Chika ma sun zuba anko duk sunje make up, Spark zuwa yayi ya dauki Naila da kansa driver ya kawo shi ya Sha shadda silver kalar takalmi da Jakar Naila,ta zuba kyau kowa ya zaci Amarya da Ango ne suke aure abin nasu yayi,Mota suka shiga sai Event center,mata da Maza har Yan school din su Naila,suna zuwa can Basma ta fito daga motar Arham jariri Yana kuka ta kawowa Naila mota,a motar Spark yace da driver Dan Allah Dan bamu waje,Driver ya fice sannan Naila ta bashi nono ya Sha,Tana gama bashi nono aka musu pics sannan suka shiga,mutane an hallara su Mima,yaro ya Sha kaya masu kyau white and silver,duk kidan Dake tashi baccinsa Jaririn yayi,kowa yaci abinda yake so anyi rawa an zubar da Naira sosai,su Chika an cashe da Beauty da Ikhy... Kamal da Amaryarsa ma sunje,ana cikin riti Mero da Haneef suka dira a Abuja amma suna hotel masauki,Mero harda cewa an kawo motar taka kuwa? Haneef yace an kawo Madam driver Yana nan zai kaimu Inda kike so,tace to Allah ya kaimu. Washe gari da Yamma suka shirya Mero an goge ta Sha kaya masu tsada Leshi kana gani kasan kayan ba karya a ciki dark green an Golden ne. Mota suka shiga driver ya kaisu har gidan Mima,Allah yasa duk sunzo Sunan Naila basu tafi ba kowa da kowa Yana gidan Mima,da yamma su Misam,Rafeeq,Arham da matayensu duk suna gidan,suna compound sai kace yau ake Sunan,Badia tazo da Anam,motar Haneef me azabar tsada ce ta shugo gidan sun zaci ma Spark ne,Sai da Mero ta fara fitowa tun daga takalminta da komai na jikinta abin a kalla ne,ba Wanda ya ganeta har takaraso gabansu tayi Sallama suka amsa,tace Mima sai lokacin Maman Rafeeq tace wace haka kamar Mero Yar aikin Maman Spark,Mero tace nice tana murmushi,Mima tace Mero kece haka ai badan kinyi magana ba babu me gane ki,suka hau mamaki,kowa sai da ya kalle ta,tace dama da mijina muke munzo Abuja ne nace bari muzo mu gaisa,Mima tace to ya fito mana ku shugo ciki sannunku da zuwa,oh Ashe kinyi aure ba sanarwa,Mero tace abin ne ba shiri shi yasa. Arham harda gulma kasa kasa ta furta Mero Yar aikin Mama mutuniyar Spark,Rafeeq yace ni naga dare Daya Allah kan yi bature yau,shi yasa aka ce ko ya mutum yake baka San me Allah zaiyi ba karka wulakanta shi amma su Mama basa ji,Arham yace ei kamar Mamanka wulakantani da take akan Ina soyayya Baki San me Allah yayi ba wlh Kinga dai Mero,dariya Maman Rafeeq tayi tace Dan banza ai Kai sai gyaran Allah. Haneef ne ya fito ya Sha gezna Yar gasken milk sai shining yake,Sai sa Ido suke yi yaran Mima,mazan ya mikawa Hannu suka gaisa matan Kuma suka gaida shi suka shiga ciki,Anam tace guy din ya hadu ita Mero Dan ubanta Ina ta samo wannan haka ikon Allah kenan daga yau na daina wulakanta Yan aikina wlh naga ishara na tuba,Arham yace kuci gaba duniya ce ai zata bi da ku,ku akan Kuna yaran General sai iskanci,ai da kunce zaku wulakanta min Basma sawa zanyi ta zazzage ku,ki duba dai Maman Spark yau suna Ina,ga Wahida sarkin bakin jini anyi bikinta tana dakin mijinta uwar tana prison,yanzu Kalli Mero dai wannan Mero da ake gani a banza ana mata kallon mahaukaciya ce ma. Basu dade ba suka fito suka musu sallama suka bar su da Cece kuce,gidan Spark suka je,Naila ta gama gyara kayan gift da komai Baki duk sun tafi har su Zarah sun tafi sabo da makaranta,Naman Sunan ma tace sai dai gobe a Kai musu,masu aiki suna ta soya nama a can compound sabo da sa ne da raguna biyu kamar me layya,Naila tana Palo ita da Goggo Sai taji sallama ta amsa,Mero ce ta shugo,Naila ta ganeta ita" tace Mero kece? Mero tayi murmushi ta shugo tace nice ta durkusa ta gaida Goggo,ta zauna suka gaisa da Naila tace ke Yar gari Ashe haihuwa kika yi? Naila tayi dariya tace ae jiya aka yi suna Mima ce ta fada min da naje,Allah ka sa Nima na sauka lafiya haka,Allah ya raya,Naila tace kema naga kamar kina da cikin Ashe da gaske ne,wai yaushe kika yi auren ba sanarwa? Mero tace Abu ne yazo cikin gaggawa,wlh ujula ujula aka yi auren nan,tare muke da shi ma Yana mota,Naila tace kice ya shugo mana,Mero ta fita ta shugo da Haneef,Naila taga miji rangadeden gaske,bayan sun gaisa tace bari na kira muku shi Yana nan,sama ta haura Spark Yana aiki a system tace kazo munyi Baki Mero da Angonta sun zo,Mero tab aure tayi? Naila tace har da ciki,yace ikon Allah,Naila tace zo kaga Mero ta goge me hali ta aura,Spark yace na tayata murna,ya mike suka fito,ahhhh bai zaici gogewar Mero ta Kai haka ba,mijin ma ya sanshi ashe ya Sha ganinsa a gidan yari in yaje ziyara,suka gaisa Sosai ya zauna suna ta hira,Naila ta kawo musu Abinci da lemuka sannan ta kawo musu Naman da ake soyawa a plate,suka ci kuwa sun Dade kafin su tafi, Haneef 50k ya bawa Naila suka tafi har mota Naila da Spark suka raka su,Naila tace sai mun zo muku muma inshaallah,Mero tace Allah ya kawo ku. Wani satin Mero da Haneef sai prison wajen Maman Spark,tayi girki lafiyayye suka Kai,bayan Mama ta fito da Yar uwarta da kyar suka gane Mero,Mama ta nuna ta da yatsa tace me...me...Mero tace nice Mero da kika ce ban dace da suna Khadija ba sai dai Mero,to ga Mero Allah ya azurtata tayi sama ke Kuma gaki a wani hali,ni bazan miki abinda kika yi min ba,albarkacin naci na Sha a gidanki baki taba hanani abinci ba bazan manta da wannan Alkhairin ba,ko nama kika ci Ina ci,tace gashi ta mika mata Daya abinci da ta kawo mata,Maman Wahida ma suka gaisa suna ta mamakin ikon Allah,Azima ce tazo suka rungume da Mero sannan Mero ta bata nata abincin,Haneef harda kudi ya basu duka,sun Dan dauki lokaci sannan suka tafi,Mero tana cewa Azima ki gaida su Goje su Scola kice bazan manta da su ba,Azima tayi dariya tace zasu ji. Naila tana yin Arba'in Spark ya dauke ta da Baby da Arham da Basma suka bar kasar suka tafi Germany,Arham sai murna yake zasu Shana,Rafeeq yaji haushi an bar Masa aikin Office a hannunsa,Misam kuwa ya biyawa Mahaifiyar Chika da Mahaifinta Makkah,ya canja musu gida me kyau. Spark amarcinsa yake Sha kawai sai da suka kwashe watanni kamar baza su dawo ba suna zaga kasashe,suna dawowa Kuma Jauro ya biyawa Yar Inna da Abba Dolo Umrah da shi kansa Jauron da iyalansa kaf,suka tafi wai za ayi addua har su Haidar da matayen su. Lokacin aikin hajji ya kusa Iman ta haifo Yarta mace kyakyawa,ba a Dade ba Hidaya ta haifi Danta Namiji itama,an Sha suna anyi shagali,Yar gidan Iman Sunan Maman Annoor aka sa mata tana kiranta da Nihad,ita Kuma Hidaya suna kawai danta ya ci Na'eem. Naila da Spark,Rafeeq da Ikhy,Basma suka tafi sauke farali gaba daya Spark ne ya biya musu,Chika alkawari yayi zai biya mata dama,can suka hadu da su Abba Dolo,Abba Dolo da Yar Inna kamar Larabawa suna makale da juna. Bayan Sallah suka dawo Mero ta Haifo Yan biyu mace da namiji kyawawan gaske kamar yaran Larabawa,kowa sai murna ake taya su,Spark ma yaje da Naila da Sha Tara ta arziki yara sunansu Nawwar da Nawwara ,su Mima sun je,Mufee da matar Kamal ma da yaron cikinsu. Sai da Basma ta Shekara biyu sannan ta samu ciki,Arham ana ta murna da kamar baza ta haihu ba itama, lokacin su Chika ma yaransu sun fara tafiya dagwai dagwai,na Naila Yana Rarrafe ko Ina,ga matar Kamal ta haihu itama Rayuwa na ja kowanne suna zamansu lafiya sai sabani Wanda ya zama dole da sauran kaddarorin rayuwa domin bawa baya zama babu kaddara da jarabawar rayuwa,cikin Basma ya tsufa itama gida ya dauke ta suka koma gaban Mima,satinta biyu a gidan da tsakar rana ta fara nakuda Arham Yana wajen aiki,Mima Bata fada Masa har suka Kai Basma asibiti ta haifo yarta mace kyakyawa,duk ba a fadawa mutane ba sai yamma likis aka sallamo su,tazo ma tayi wanka aka yiwa jaririya wanka suka shirya tsaf ta gwada bashi nono,Arham sai wajen dare yazo gidan ganin matarsa yaya take,Mima ya gani yace Basma fa ya jikin nata? Mima tace tana daki shiga mana ka ganta,Yana shiga ya ganta da jariri a hannu tana cin Abinci,Arham yace wai haihuwa kika yi? tana dariya tace gashi ka gani kuma,ya dafe kirji yace wayyo dadi, Alhmdllh Alhmdllh,Mima tana jinsa Yana hauka iri iri,na zama Daddy wannan yarinyar zata ga muzurai ince ke shiga gida,dariya Basma tayi tace ni Kuma nace wato baza ki shirya ki tafi school din ba sai kin makara wannan yarinya Allah ya shirye ki bari na fadawa Daddy,sai na kwala ma kira Daddy Daddy,Arham harda kausasa Murya na'am lafiya,ka zo taki ta shiryawa ta tafi school,sai na fito na mata wani kallo tuni Zata kama gabanta,dariya suka yi sannan ya zauna ya dauke ta yace a'a Kai nayi 'ya kuma ni,Anya zan iya bacci ma,Basma tana ta dariya,Mima ta sanarwa dangi da kowa. Su Arham sunga jama'a kullum cika akeyi yayye da sauran dangi da abokan arziki,ranar suna yarinya taci Sunan Mima suna kiranta da little Mima,Mima an Maida sunanta sai farin ciki take yi sosai yarinya tana gani gata,Papa yace matarsa guda ai sai abinda take so a duniya. Azima kuwa ta Jikin katanga ta fadawa su Scola sakon Mero har yanda tayi kyau da Wanda ta aura,Goje yace mu dai mun shiga uku ko wacce muka Shaku da ita sai ta bar gidan yari ta auri me kudi daga yau baza mu sake kula ko wacce ba duk kuje Yan iska Shegu,'ya'yan mutanen banza ,kana shakuwa da mace sai kaji fit ta fice tayi aurenta,Dan Indo yace abin bakin cikin ma sai kaji Dan prison ne,yanzu dai ji Tantiriya da wannan Dan iskan Spark shege Dan giya,Scola suka sheke da dariya yace Spark dinne Dan giya? Da mene idan ba Dan giya ba Yana magana Yana lumshe Ido kamar zaiyi bacci in ba giya yake Sha ba ubansa Soja yake Sha? Marar neman Albarka,suna ta dariya Scola yace kaji ance ta haihu ma Naila,Dan Indo yace ta haihu? aka ce tsohon zance yace a gidan yari a Nan ya mata ciki,da abinta ta shiga gidansa,daga Dan auren har ta haihu a nan yayi mata ciki karya suke,scola suka dinga dariya da ihu,Dan Indo yace ana kallonta a namiji Ashe shi harka kawai yake Kwasa Allah wadaran Spark kaji, ban taba ganin Dan iskan yaro ba irinsa,suna ta dariya,Malam Jilani Yana zaune yace wallahi Haramun kake aikatawa ranar lahira wlh sai ka Bada shedar abinda ka fada an rubuta,Dan Indo yace Kai rufe mana baki munafukai duk ba da ku aka hada baki ba,Kun fake da karatu,kasan kana fadar gaskiya kazo ka fada mana macece tun farko mana,sai anyi magana ka makale Murya kamar zaka yi amai wai ke Balarabe munga Sudais da Shuriem ma karewa,gashi Nan sauran Yan uwanka malamai sun fita sun barka,su Malam Garzali Kai kana Nan sai ka Kara wata uku sabo da bakin hali,Malam Jilani yace Kai yaushe zaka fita? Kai da aka yanke Maka hukuncin daurin rai da rai,shuru suka yi Dan Indo Yana Jan Kwafa. Abba da Yar Innar sa suna zaman su lafiya,sana'arsa sai yaga dama ma yake yinta yau rana tana takewa ya gudo gida yayi kwanciyarsa,yaki fita sai Aslam ne ya zauna a shagon ya siyar, Yar Inna tace baza ka fita ba kenan? Yace bazan siyar ba na gaji Wanda ya dogara Dani ma a unguwa ya dogara da aikin banza,in zai kama me sana'ar arziki ya kama ya dinga siyen kayan masarufinsa a can,ni na gaji da auna hatsi nauyin tsiya,sai ka jawo buhu ga nauyi ka zuba a daro,wajen kamfatowar ma ba arziki sai nauyi duk kasusuwana sun fara budewa,sai damatsa nake ajiyewa sai kace Dan dambe,Yar Inna tayi dariya kamar me tace Ina kaga wasu damatsa,in ma kayi damatsa ai haka ake so,ke Yar Inna ki rage budurwar zuciya so kike Naila da Hidaya na auren masu damatsa kema kice irinsa kike so na koma,shi yasa wato naga kin yarda da sana'ar lokaci guda,Yar Inna tace Allah ya kiyaye Kai yanzu ko Gym kake zuwa Ina zaka tara damatsa,Abba ya kwanta ya mimmike yace wayyo Hashimu kwanta ka huta. Annoor da Iman dinsa suna joint na Shan Ice cream da shawarma,aka kawo musu suna zaune,Baby tana cinyarta ya shiga bawa Iman a Baki tana ci suna hirarsu ta masoya,Ice cream din yake bata tana Sha,sai wani ya fado fuskar yarsu har da rige rigen lashewa a fuskar yarinyar,ya riga Iman lashewa,hannun ta doke tana shagwaba tace ka min wayo Allah dariya yayi yace ni da 'yata kin tsaya kina yanga,wajen kida na tashi harda rawa da hanu Yana bata tana cin shawarma abinsu sharr. Nabeel tare da Hidaya suna gidan Haidar,Haidar dinma Yana Nan suna ta hira abin su a gidan suka yini. Su Nabeela ma sun haihu suna zaman su lafiya da mazajen su suna zumuncinsu. Mero tana Jikin mijinta a bedroom suna hutawa,tace wai Ina Yar uwarka Ihsan ne?yayi murmushi yace tana Nan Kano tana aikinta ta rasa mijin aure har yanzu,ita Kuma auren take so yanzu hankalinta ya dawo jikinta amma ta rasa mijin,taje Adamawa ta dade ta dade ko zata dace amma Ina,ta dawo Kano duk yawan Al'ummar Kano ta rasa mashinshini duk ta rame to karshe dai abokina Yana sonta yanzu zo Kiga murna zai Kara ta biyu da ita,Mero tace maganin marar hankali kenan duniya makaranta,shi yasa in mutum yace shi duniya ya sa a gaba to zai ga duniya,dariya suka yi yace Allah ya kyauta ya raba mu da aikin dana sani ya ja musu Bargo suka shike suka fara soyewa. Misam ne ya dawo daga Office ya Kalli Chika dinsa ta Sha wanka,daukanta yayi Yana zagawa da ita a parlon,Baby na binsu da kallo Yana dariya,hannaye ta daga tana tsalle har da kuka itama a dauke ta,Chika ya ajiye ya dauki yarsa Yana shilla ta tana dariya,chocolate ya bare ya bata yace Chika ta shirya suje gidan Rafeeq,bayan yaci abinci suka tafi gidan Rafeeq,suna zuwa Rafeeq yace Kai 'Yan anace yau ma an kawo min ziyara kenan ku baza ku dinga bari Ina hutawa ba,Chika dariya tayi tace wlh zamu daina zuwa ma,Ikhy tace kyale shi kawata ni da zaku dinga zuwa kullum ma ai nafi son haka wlh,Arham ne suka zo da Basma da Baby suma,Rafeeq yace Nidai an nace min kowa sai dai ya taho gidana,Arham yayi dariya yace dama biyowa muka yi mene da Kai da za a nace Maka,kaga abar nacewa ya nuna Basma dinsa yace itace me abin bayarwa ba Kai ba,dariya suka yi cike da nishadi,Misam yace sarkin Kwalbewa an Lula duniya sai abinda Hali yayi,Bado yaga ta kansa cewar Rafeeq,cike da nishadi suke hirar su. Spark kuwa Naila tana samun hutu ya dauke ta suka bar kasar tare da Baby dinsu,suna jirgi suna daukan pics cike da nishadi,Baby Yana ta kiriniya gwanin sha'awa,Naila wata ta Gani a jirgi babbar mace tace Dan Allah dauke mu ta bata wayar matar ta dauke su pics da videos sunyi kyau,Naila tace Kalli yanda muka yi kyau ya Kalli pics din ya mata rada a matse nake Baby uwar Baby matar Baby ta Baby da Babynta Kuma gata Baby itama muna sauka a bani bado,dariya tayi tace Ina Jin wannan kirarin nasan me ake so dai, yayi dariya Yana tuna masifar Naila lokacin tana da ciki ya dinga dariya Yana tuna mata itama dariyar take,tace wlh in na tuna dariya nake yi,Kunnenta ya ciza kadan sannan yace Allah ya barmu tare,tace Ameen Baby Mijin Baby Baban Baby,dariya suka yace Ameen Ameen Allah yasa ko wata na Gani idan zanje zance nayi makuwa nayi batan kai na dawo gida wajenki,Naila ta sheke da dariya tare da furta Ameen. INA BAWA FANS DINA HAKURI BISA MATSALA DA AKA SAMU A WAJEN POSTING. WANNAN LITTAFIN NA SAMU MATSALAR TYPING WLH BAN YI SHI CIKIN DADI BA,SABO DA YAZO MIN A BANI DA LAFIYA,GA ZUWA ASIBITI LOKACIN DA AKA SHIGA BOOK2 HAR KUSAN FARKON BOOK3,A BOOK3 KUMA UZURI YA SHIGO MIN DA YAWA BA ZATO WANDA YA JAWO DELAY DA YAWA A LITTAFIN,BAN JI DADIN HAKAN BA SABO DA KOWA YA SABA BANA BOOK HAKA A DADE BA A GAMA BA SANNAN BANA FASHIN POSTING SAI DA DALILI ME KARFI,WANDA A WANNAN BOOK DIN HAR NA GAJI MA DA BADA UZURI,BANA FATA NA SAKE TYPING ME DELAY HAKA,NI KAINA BANA JIN DADI WLH AMMA DUK DA HAKA ALHMDLLH INA GODIYA GA ALLAH DA YA BANI IKON KAMMALA WANNAN LITTAFI LAFIYA DA NI DA MASOYA WANNAN LITTAFIN TANTIRIYA A GIDAN YARI. INA MIKA GODIYA TA GA DUKKAN WANDA SUKA SIYI LITTAFIN NAN MAZA DA MATA,SUKA SA KUDIN SU SUKA SIYA INA MATUKAR GODIYA ALLAH YA BIYA MUKU BUKATUNKU BAKI DAYA,ALLAH YA YANTA KU CIKIN YANTATTUN BAYINSA A WANNAN WATA MAI ALBARKA DA ZAMU SHIGA. CIKIN SAURI NA KARASA WANNAN LITTAFI KASANCEWAR AZUMI YAZO WATAN IBADA. WANDA SUKA JAJIRCE DA YI MIN SHARHI KO YAUSHE HAR MUKA GAMA NOVEL DIN NAN WLH BAN SAN MA DA BAKIN DA ZAN GODE MUKU BA MUSAMMAN BABY AK AMINA YUSUF BAWALE HAJJORA INVESTMENT MURJANATU ABU NA BANGA DA DAI SAURAN SU INA GODIYA. SANNAN WANDA SUKA JAJIRCE MA FARKO HAR AKA YI NISA UZURI YA SHUGO MUSU INA GODIYA,DA SAURAN WANDA BASU SHARHI BA KUMA INA KAUNAR KU NA GODE MATUKA. MASU JIRAN COMPLT KUMA DA KUKE GEFE NA GODE. ALLAH YASA MUYI IBADA KARBABBIYA. ALLAH YA BAMU LAFIYA ME DORARRIYA ME AMFANI BAKI DAYAN MU INA YIWA KOWA FATAN ALKHAIRI MASOYA. AsmaBaffa