[9/9, 9:04 PM] +234 806 222 4030: Cikin tsananin tsoro da mamaki. Maryam ta rumtse idanunta da azaban k'arfi tare da cewa. "Innalillahi waInna'ilaihirajiun. Zaleeha kashe kanki zakiyi baki da hankali ne?." sai kuma duk falon ya ricab'e sabida. Ihun da Zahira keyi tanayi tana tsalle da burburwa tare da cewa. "Shike nan ai an huta." Aunty Lubna kuwa da Ziyada ruggume juna sukayi tare da rumtse ida nunsu, Ganin yadda Zaleeha tasa knife d'in ta yanke wuyan hannunta tare da kurma ihu mai gigitarwa, tuni jini yaketa tsiyanyowa yana zubowa har k'asa. Cikin wani irin tsoro da al'ajabi da firgici ya Ahmad yayi sauri ya k'arasa gabanta, tare da sa hannu ya fizge knife d'in data saitashi kan jijiyar mak'ogoronta. Ihun Mama da Yayarta Ruda da Zahira ya cika gidan gaba d'aya. Mamy da Aunty Lubna da Ziyada ma kukan sukeyi mai cike da tsoron ganin Zaleeha zata aikata kisan kai. Ga kuma ihun da itama Zaleehan takeyi tanayi tana tsalle tana. "Wallahi zan kashe kaina! gwara in mutu kowa ya huta! In yaso in na mutu a raba gawata biyu a kai musu dukansu biyu kowa a bashi tsagi d'aya." Ya Ahmad kuwa hannunta data yanke yaketa kamowa dan ganin yadda jini ke zuba alamun ta yanke sosai. Baba Malam kuwa tun sanda yaga ta yanke kanta, ya juya ya bar wurin yana tafe jiri na fizgarshi sabida tsananin tashin hankali da b'acin rai. A gabanshi a gidan shi ƴarshi ke kirari da tutiyar kashe kanta, a kan mijin da itace tace ya turo iyayenshi. Gaba d'aya idanunshi basa gani, sabida wani fitinennen duhu daya mishi k'awanya kan kwayar idanunshi, babu abinda yakeyi sai sunan Allah yake ambato, Wai yau shi Malam Bashir Sulaiman Dukku shine za'ayi kisan kai a cikin gidanshi, kuma yarsa ce ta cikinsa, lallai fulani sunyi gsky da sukace, (Te'ud'o laddefu and'i dayan sabere) kowa ya auri daji tofa yasan tabbas wata rana zai haifi Saura/lampo. Jiki na rawa ya zauna dirsham a bakin gadonshi tare dasa hannu duka biyu ya tallabe kanshi kana yaci gaba da zancen zuci. "Eh tabbas yau dai yaga zahiri, ashe ba banzaba Fulani keda k'abilanci a fagen neman aure da bada aure, yau gashi yaga illa da kuma dafin gwamutsa zuriya, sabida ai dai kowa ya sani abinda d'iyarshi Zaleeha take inkarin zata aikata koma yace ta aikata kafurcine wanda addinin musulunci yayi tir dashi, kisan kai ko kashe kai al'adace ko d'abi'ace ta kafurai marasssa imani da tawakkali wanda basuyi imani da Allah da manzonsa ba, bare suyi imani da k'addara mai kyau ko akasin haka." Wani irin fitinennen kukane mai cushe zuciya da numfashi ya kwabcewa dottijon nan mai cikar haiba da kamala, mik'ewa yayi cikin tsananin kuka ya d'auki yar karamar jaka, Qur'an da wasu littafan ya saka a ciki, sannan yasa ATM nashi da carbinshi kana ya d'auki car key d'inshi. A hankali ya nufi cikin gidan inda yake jiyo ife-ifen na k'ara tsananta, Dib-dib-dib haka zuciyarshi ke bugawa da tsananin k'arfi da firgita Kardai ta kashe kan nata ne?. Yana isa ya samesu gaba d'aya suna tsaye a tsakar gidan, sai Zaleeha daketa kwaso akwatunan da yan uwan Abdussalam suka kawo tana ta watsosu tsakar gida, gaba d'aya tayi kaca-kaca da komai ta birkice ta zama kamar mai shafar al'janu. Ya Ahmad ne keta kamota tana zillewa duk ta birkice gashin kanta yayi biji-biji ya hargize ta zama kamar zarerriya Wani k'aton akwati ta jawo wanda wlhi ko maza zai sunyi da gaske zasu jawoshi sai gashi ta figoshi ta turoshi waje, Ahmad ne yayi sauri tareta cikin gigita da kid'ima ya kamo hannunta dake zubda jinin tare da cewa. "Wallahi al'janine a jikinta, sune suke sata yin komai." Da sauri ya sake hannunta ya kalli Ziyada data ruga a guje ta nufi mahaifin nasu, tana zuwa ta durk'usa gaban Baba malam hannu duka biyu ta d'ago cikin tashin hankali ta saki kuka mai sauti tare da cewa. "Dan Allah Baba Malam kayi hak'uri, kada ka tafi, in ka tafi ka barmu ya zamuyi, dan Allah Babana kayi hak'uri, wlhi gwara ka kori ita Zaleeha tunda bazatayi maka biyayya ba." sai kuma ta kifa kanta bisa rumfar sawunshi cikin neman al'farma. Hakama Maryam da gudu tazo gabashi ta durk'ushe murya na rawa cewa. "Wayyo Allah na wayyo Ya Ahmad ka bar Zaleeha kaga zata kashe mana mahaifinmu da bak'in ciki." Sai kuma ta matso gab dashi cikin tsananin kuka take magiya. Tuni Ahmad ya mance da Zaleeha bare matsalarta yazo tsakiyar k'annenshi suka durk'usa gaban Mahaifin nasu suna kuka mai tada hankali. Zaleeha kuwa sam bata cikin nitsuwarta bare tasan illar abinda take aikatawa asirin da uwarta tayi mata ya shafe nitsuwarta burinta kawai ta firgita kowa a fasa batun aurar da ita. Ido Baba Malam ya rumtse ganin Mamy ta motso gareshi cikin kuka take cewa. "Kada laifin mutun d'aya ya shafemu baki d'ayanmu, idan ka tafi ya zanyi da rayuwata? ina zan shiga? Me ya rage min da zaman gidannan? Dama d'ana kwaya d'aya tak Allah ya bani, shi kuma ba'a gidan yakeba, dan k'ashin Kanka ne da aurenka nake zaune a gidan nan, ni banyi maka laifiba Maryam batayi makaba hakama Ziyada da Habu da Zakiriyya to meyasa zakayi nesa damu akan laifin da bamu aikata ba?." ta k'arishe mgnar tare da durkushewa gefenshi kana ta kamo hannunshi murya na rawa tace. "Duk in da zakaje sai ka tafi damu, in kuma laifinsu ya shafemu ne, wlhi kana fita nima zan bar gidan nan." kalamam Mamy sunyi matuk'ar k'ara gigita su Maryam kawai sai suka saki sabon kuka. Mama kuwa da Ruda da Zaleeha ihu sukeyi wai bak'in ciki ya haukata Zaleeha. Daga bakin Gate Habu ke jiyo ihu da hargitsin dake cikin gidan nasu, Ko parking bai gama dai-dai tawa ba ya fito cikin motar, a guje ya nufi cikin gidan nasu gaba d'aya jikinshi kerma yakeyi. Wani irin tsayuwa yayi tare da zaro idanunshi baki d'aya, kuka da magiyar dasu Maryam keyi ya ganar dashi abinda ke faruwa. Wani irin tafasa da harzuk'a zuciyarsa keyi, juyowa yayi tamkar zautacce, Zaleeha da ta Kikimo wani akwatin ne ta harboshi, dai gaban Habu, kana ta juya tayi hanyar shiga parlour da niyar kwaso wani. Wani irin razanannen k'ara ta saki jin wani irin azabebben naushi da Ya Habun nata ya d'irka mata a tsakiyar gadon bayanta har saida tayi tangal-tangal zata fad'i k'asa, bata gama gigitar naushinba taji yasa k'afarshi ya tareta daga fad'uwar da zatayi ya naushi k'irjinta wanda saida ta bada sautin hak. bata ida tsayuwarba tayiji yasa k'afarshi ya tad'eta ta yi k'asa, ji kake gib ta bugi k'ofar parlour tayi gaba ta dawo baya, sai kuma ya zaro belt d'in k'ugunshi ya juya kan belt d'in dai-dai inda k'arfen yake ya fara tsula mata tamkar Allah ya aikoshi. Ihu da karaji ta sake tare da fara mirginawa tamkar macijiya tana. "Wayyo Ya Ahmad ya Habu zai kasheni! Wayyo goshina ya fashe! Wayyo k'uguna ya karye, wayyo Allah na na mutu na lalace". Shi kuwa binta yakeyi a baya yana had'a mata naushi da gula da zana tare da magana cikin haki dake nuna tsantsar tafasar da zuciyarsa keyi. "Shegiyar yarinya. tsinenniya mara amfani a doron duniya, kiyi ihu da kyau ki fad'a da k'arfi kasheki zanyi, tun kafin ki kashe mana mahaifinmu, kasheki zanyi koda ma rage mugun iri, shegiya mai zuciyar arnan kan duwatsu. Shegiya mai gadon bak'ar zuciya." Ina Ahmad, Maryam, Mamy, Ziyada su bata Zaleeha sikeyi ba bare su ceceta daga bugun gardi da Ya Habu keyi mata. Ganin alamun habu zai kasheta ne yasa Mama tayi tsalle tare da shiga tsakaninsu, da k'arfi ta ingiza Habu baya tare da cewa. "Dan ubanka kai farar zuciyarce da kai? Nace kai ɗin farar zuciyar ce da kai? da kake cewa tayi gadon bak'ar zuciyar a ina ta gado kenan?." Kan Zaleeha ya kumayi sunkuyowa yayi yasa hannu ya damk'o wuyanta tare da shak'ewa da k'arfi kana ya kalli Mama tare da cewa. "Eh nima bak'ar zuciya gareni kuma, data kashe mana uba gwara na kasheta, bak'ar zuciyar kuwa a ina zamu gada banda wurin bak'ak'en arnan iyayenkin can dake bautar gumaka." Aunty Lubna ce tayi k'arfin halin kamo hannun Habu da niyar cotar rayuwar Zaleeha daketa kakarin mutuwa tuni idanunta sunyi zuru-zuru a woje, sai kuma ya jiyo muryar Baba Malam na cewa. "Abubakar ka dawo haiya cinka, kisan Kai ya sab'awa addinin musulunci." jin haka yayi matuk'ar sace mishi zuciya hakan yasa ya hankad'e Zaleeha, kana yazo ya durk'usa gaban mahaifin nasu cikin rauni yace. "Dan Allah da al'farman manzon rahma Baba Malam kayi hak'urki ka gafarcemu ka rufa mana asiri kada kayi nesa damu." Ita kuwa Zaleeha wani irin azabebben tari takeyi tun sanda Habu ya sake mata wuya tarin takeyi tare da kuka, Aunty Lubna ce ta ruggumeta sukaci gaba da kuka a haka, Ruda kuwa tunda Habu yazo ta silale ta bar gidan dan tsoron yaron take. Ita kuwa Mama akwatuntan su Abdussalam d'in ta fara tattarewa tana maidasu parlournta. Shi kuwa Baba Malam kanshi ya jujjuya tare da rab'awa gefen su da nufin zai fita, ganin hakane yasa fargabansu ya ninku sama da sau d'ari, Maryam ce ta kife kanta a k'asa cikin kuka tace. "Kaito na! Kaiton rayuwata da bani da damar share hawayen mahaifina, Yau da ace bani da aure wallahi da na sharewa maka hawayenka baba malam Kodako Saifuddeen kurmane makahone gurgune kuturune wallahi matuk'ar zakayi farin ciki tabbas da zan zauna dashi. Inama ana rabuwa biyu wallahi da na kasu biyu." Ziyada ma kukan takeyi tare da kamo hannun Baba Malam cikin rauni tace. "Baba kada ka tafi ka barmu, in yana sona ni zan zauna dashi." Gaba d'aya sun rud'e da kuka hatta habun kuka yakeyi bare kuma Maryam da Ahmad masu rauni. Wani irin Murmushi Ahmad yayi still hawayenshi na kwaranya, kai ya jinjina ganin Zaleeha na rarrafe tamkar yarinya k'arama a hankali ta isa gaban Baba Malam hannu ta had'e wuri d'aya cikin yanayin neman gafara, murya na rawa jikinta na kar-kar-wa numfashinta na ficewa ba komawa, cikin shak'k'k'iyar murya a disashe tace. "Na amince Baba Malam na yarda ayi auren ka aura min Saifuddeen d'in na amince. Ka yafe min Babana ka gafarta min ka rufa min asiri kada in hallaka sabida fushinka na amince ayi auren na yarda." Da sauri Maryam da Ziyada suka ruggumeta. Ahmad da Habu kuwa ruggume juna sukayi, Mamy kuwa kamo hannun Baba Malam d'in tayi ta nufi side d'inshi dashi, shi kuwa ba musu ya bita. Ahmad da Habu sukabi bayansu, Aunty Lubna kuwa kamo hannun Zaleeha tayi ta nufi Side d'in Mamy kana Ziyada da Maryam sukabi bayansu. Zahira kuwa da sauri tabi bayan Mama. A gidan Saifuddeen kuwa, Ummi ce zaune a parlournta ita da. Su Bappa Ali da Malam Ashiru. Cikin nitsuwa tayi musu bayanin dalilin nemansu da tayi ta k'ara da cewa. "Hankali na ya tashi tun zuwansu na forko, yarinyar ta nuna bata son auren da Saifuddeen ta gaggaya musu bak'ak'en maganganun da suka gigitasu suka tayar musu hankali, anan Ahmad ya dawo yana kuka cur-cur da hawayenshi dan wulak'ancin da tayi musu ita da aminanta. basu b'oye min komai ba, sai dai shi Saifuddeen baiso su sanar min ba sabida tsananin son yarinyar yakeyi ita kuwa bata sonshi ina tsoron kada tazo ta cutarmin shi." Ta k'arishe maganar cikin yanayin tsantsar karaya da tsoro. Bappa Ali ne ya gyara zama tare da fuskantarta da kyau kana yace. "To yanzu me kike so ayi?." Nannauyan ajiyan zuciya ta sauk'e tare da cewa. "Ni dai auren ya fita raina, ku kira Saifuddeen ku taushi zuciyarshi ya rabu da yarinyar ya janye batun auren, kana kuje ku sanarwa iyayenta cewa an fasa batun auren tunda yarinya bata so gwara a bari kawai, magnin bari kadama a soma." Baba Ashiru ne ya katseta da cewa. "A,a sam bamu da hujjar janye batun auren nan, da girmanmu da mutuncinsu munje munyi magana gemu da gemu sannan dan zancen baya muce zamuje muce mun fasa auren. Sannan keda kankifa kika ce mana Saifuddeen yana son yarinyar matuk'a gaya." Cikin sanyi ta girgiza kai tare da cewa. "Ba zancen bayan kadai bane. Ko shekaran jiya Hayatuddeen yaje gidan kakarsu wurin Abokinshi k'aninta ya sameta can tanata kuka, wai ita bata son auren gurgu kurma. Tayi al'washin in dai aka aura mata shi zata kashe kanta. Kuma jiya ma dasu Saifuddeen d'in sukaje nanma ta ciccimusu nutunci sun dawo nan suna mgnar basu san na jisu ba." A hankali Bappa Ali yace. "Ba komai! In sha Allah babu abinda zai faru sai al'khairi! Ke dai kiyi ta addu'a kin san addu'ar uwa karb'eb'b'iyace domin bata da hijabi, Tunda kin sani mun sani Saifuddeen yana sonta tofa mu bisu da addu'a. in har bata so ai iyayenta zata sanarwa kuma in bata sonshi baza bashi izinin turamu ba." kasake tayi tana jinsu, suna bata k'arfin guiwa, cikin kula Malam Ashiru yace. "Kinga fa du-du-du kwana biyar ne ya rage bikin ta yaya zamu fito da wata matsala ta b'angarenmu, muyi hak'uri in har bata so d'in su sa fito da matsalar." Kai ta jinjina tare da cewa. "To tunda kunce haka ba matsala, amman ni naso Saifuddeen ya nemi matar aure a cikin tarin matan dake bibiyarsa da soyayyarsu. Amman ba komai Allah yasa hakan shine mafi alkairi." Amin Amin sukace baki d'aya, kana sukace to su zasu koma dukku. nan suka sallemi juna suka tafi. A can gidansu Zaleeha kuwa, shiru gidan ya koma kamar gidan zaman makoki, kowa da abinda ke ransa, su Ahmad da Mamy da Maryam dai sunyi ta magiya da rok'on Baba malam da bashi hak'uri. Har saida suka ga alamun ya samu sassaucin tashin hankalin da yake ciki. Bayan anyi sallan isha ne. Malam Adam da Ya Aminu suka shigo gidan a jere. Kai tsaye parlour Baba Malam suka nufa, Bayan sun gaisa ne ya musu bayanin abinda ya faru. kwaffa ya Aminu yayi dan tabbas da yana nan to da tuni ya karya Zaleeha. Shi kuwa Malam Adam kai ya jinjina cikin tsananin mmki da tsoron yaran zamani yace. "Aminu je ka kirawo min Zaleehan." To yace kana ya mik'e ya nufi part d'in Mama. Ita kuwa Zaleeha zuwa yanzu dai tayi kuka har hawayenta sun kafe. Da kyar Aunty Lubna da Maryam suka sata tayi wonka kana tayi salla, sannan suka bata magani ta sha, domin tuni wuyanta ya kumbura haka fuskarta ,gaba d'aya jikinta ciwo da tsami yake mata duk farar fatar nan tayi jazir ga tsami da yankan da tayiwa kanta yayi duk da anyi mata dressing. Rumtse idanunta tayi lokacin data rab'a jikin Ya Ahmad da yanzu ya shigo, wasu zafafan hawaye ne masu k'una suka kwaranyo mata. sosai ta zama abar tausayi dan duka iya duka Habu ya jibga mata gashi ita da kanta can ƙasan zuciyanta take jin zafin abinda ta aikatawa mahaifinta. cikin sanyin murya da tausayawa tare da lallashi Ahmad yace. "Zaleeha!." bata amsa ba sai wasu sabbin hawaye ne suka fara sintiri a fuskarta. Lubna ce tasa tafin hannunta ta share mata hawayen, yayinda Maryam ma idanunta sukayi rau-rau alamun zasu zubdo kwalla, muryar Ya Ahmad d'in nasune ya katse musu shirun nasu. "Dan Allah Zaleeha na rok'eki da girman Allah kiyi biyayya ga umarnin mahaifinmu, kiyi koyi da Maryam, ki kare mana mutunci da martaba da darajar gidanmu dana mahaifinmu." A hankali ta bud'i baki cikin disashewar murya tace. "Ya Ahmad bana sonshi wallahi na tsaneshi ji nakeyi kamar zan mutu in na tunoshi." kanta ya shafa tare da cewa. "Zaki soshi, zaki daina jin komai, in kin rabu da aljanin dake jikinki. Ni nasan Zaleeha tana son farin cikin Babanmu." Shiru tayi dan ta fahimci ya Ahmad dai ya maidata mai aljanu so bazai tab'a fahimtar matsalarta ba, shi kuwa d'agota yayi suka fuskanci juna cikin tausaya mata yacee. "Dan Allah Zaleeha kiyi biyayya ga auran da Baba Malam zai miki ki zauna d'akinki, nayi miki al'k'awarin zan miki duk wani abu da kikeso a duniya matuk'ar baifi k'arfina ba, kuma bai sab'awa shariya ba, ki gaya min duk abinda kikeso zan miki shi k'anwata, ni dai fatana a miki auren ki zauna lfy da mijinki." cikin zubda hawaye tace. "Ka saya min sabuwar mota, motocina su zama biyu." da sauri Maryam tace. "Ai yanzuma motocinki biyu ne, ai kayan aurenma da motarki sabuwa fil Saifuddeen ya had'o miki." Ido ta rumtse da k'arfi dan wani d'aci da takaicin jin sunanshi da Maryam ta kira cikin had'e fuska tace. "Bana son wannar, abin gori abin dangin miji". murmushi Ya Ahmad yayi tare da cewa. "Zan saya miki k'anwata sabuwa fil zan saya miki, motocinki su zama uku." sosai taji dad'in amincewar da yayi zai saya mata mota, ganin taji dad'i yasasu jin dad'i suma. Ahmad ne ya rik'o hannunta tare da cewa. "Da me kuma kike so?." cikin jin dad'i tace. "Sabuwar system." cikin jin dad'i fa da ganin yarintarta yace. "Kin samu." kayan d'aki kuma wanne iri kikeso." jim ta d'anyi tare da cewa. "Ko wannema." a tunaninta me zata ce a kan kayan d'aki abinda ko sun kashe kud'i sun mata bazata soshiba. haka fa sukayi ta lallab'ata. Ya Aminu kuwa yana isa parlour Mama ya samu, Habu cikin had'e fuska yace. "Ina Zaleeha tazo, Baba malam na kira." "Tana part d'in Mamy." "Je ka kira min ita." to yace kana suka nufi parlour Mamy, daga bakin k'ofa ya tsaya tare da cewa. "Ke Zaleeha maza ki zo, Baba Malam na kira." jin muryar habu yayi masifar razanata, da sauri ta mik'e ta nufi parlour. Ahmad d'inne yabi bayanta. ganin Ya Aminu da Ya Habu a parlour'n ya k'ara firgitata. nur-nur tayi gaba sana suka bita a baya, tana tafe tana d'ingisa k'afarta. har suka isa parlour. kana Ahmad na biye dasu a baya, A hankali ta isa gaban Baba Malam d'in jiki na rawa ta durk'usa ganin yadda ya Aminu ke watsa mata harara yasa tayi maza tayi k'asa da kanta, murya na rawa tace. "Baba Malam gani." shiru yayi yana k'are mata kallo, gaba d'aya jikinta rawa yakeyi, Malam Adam ne ya kalleta tare da gyara murya wanda sai lokacin ta ganshi, cikin rawan murya tace. "Daddy ina wuni." ido ya lumshe tare da cewa. "Lafiya lau Zaleeha." daga nan sukayi shiru na tsawon 55 seconds sannan Malam Adam ya kira Zaleeha wacce tsoro ya hanata salama. "Na'am". A hankali ya fara magana. "Naji abinda kikayi, da kuma abinda kike Al'washin yi na cewa zaki kashe kanki ko?." shiru babu mgna sai wata zazzafar zufa data keto mata, "To yanzu gaya min cikin mutun biyu da kika sa suka turo mana iyayensu wa kike so?." kai ta jujjuya alamun babu. Cikin fad'a Aminu yace. "To uban wa yasa zaki had'a mana kayan mutun biyu, kin san aurenki saura kwana biyar meyasa zakisa Abdussalam turo iyayenshi." da sauri tace. "Bani bace nace su kawo kayansu bafa." a hatsale Habu yace. "Waye to." cikin tsoro tace. "Mama ce." shiru sukayi sai Baba Malam ne yace. "Uhummm". Malam Adam kuwa yace. "To yanzu dai gwara mu zare hannunmu a kanki, gwara mahaifin naku ya tafi ya barku kiyi duk yadda kika ga dama ko." cikin raunin murya tace. "Dan Allah, Baba Malam kayi hak'uri na tuba, ku gafarceni, Kayi hak'uri kada ka tafi, na yarda ayi auran." cikin jin dad'i Malam Adam yace. "Allah ya miki al'barka, tashi kije." jiki na rawa ta mik'e ta tafi. daga nan suka ci gaba da tattaunawa. Nan Baba Malam ya bawa Habu umarnin cewa gobe da safe ya kwashe kayan su Abdussalam ya mayar musu. Ita kuwa Zaleeha d'akinta ta wuce, kana ta d'auki wayarta. 10:15 pm ta gani, zuciyarta cike da bak'in ciki ta kwanta, text tayi ta rubutawa da mugayen kalamai tana tura mishi har kashi uku, sannan ta kira Bilkeesu ta gaya mata duk abinda ya faru, nan bilkeesun tace. Tana zuwa gobe dan mgnar bazata yiwu a waya ba. Saifuddeen kuwa, kafin ta tura mishi texts d'inma yayi bacci sabida a gijiye yake. Washe gari tun da sanyin safiya, Ahmad da Salisu suka shigo da masu gyaran gida, dan sabunta fentin gidan. Kai tsaye sashin wannan part guda biyun nan wanda yakeda ciki da parlour da dinning area, a tsakanin part d'in da komansu iri d'aya suka nufa. In da nan Raliya da Ahmad suke a d'aya part d'in. Nuna musu duk gyaran daya dace sukayi kamar farfasa steps d'in tsakanin parlour da dinning area, yadda wheelchair D'inshi zaibi ko ina a part d'in har zuwa cikin parlour'n nan mai 2 beedroom dan nanne zai zama turakarshi. Suna gama nuna musu suka fara aikinsu,. Su d'in kuwa kai tsaye cikin gidan suka nufa, jin shiru parlour ba kowa yasa suka wuce parlour Saifuddeen, suna shiga suka hangoshi kan wheelchair d'inshi mai azabar kyau. Ya bawa k'ofar shiga baya. Ba jin takunsu zaiba bare yasan akwai mutane a bayanshi, Wayarshi ya zubawa ido yana maimaita karanta text d'in da Zaleeha ta turo mishi a karo na barkatai. Wani irin zaro ido Ahmad yayi lokacin da idanunshi sukayi arba da abinda ke rubuce a wayar, wani irin zazzafan numfashi ya sauk'e da k'arfi tare da...! Littafina na kuɗine in kin karanta na sata kin san sauran in kina ɓuƙata turo katin mtn na raɗi uku kacal ta wannan number 09097853276 ko kuma ki biya ta asusuna na 0005388578 jaiz bank Aisha Aliyu Garkuwa. By *GARKUWAR FULANI* [9/9, 9:04 PM] +234 806 222 4030: Zazzafan numfashi ya sauƙe, da ƙarfi ya fusge wayar daga hannun Saifuddeen, sosai hankalinshi ya tashi ransa yayi mummunan ɓaci dan ganin kalaman da Zaleeha ta rubutawa Saifuddeen tacikin text message, wani irin ɓaƙin ciki da ɓacin raine suka tokarewa Ahmad maƙoshi, shikam baisan meyasa Saifuddeen ya maƙalewa Zaleeha ba, yarinyar da bata ganin mutumci da ƙimarsa ko kaɗan, yarinyar da ta maida rashin kunya man shafawanta. Ɓata fuska Saifuddeen yayi tare da miƙowa Ahmad hannu, alaman ya bashi wayarsa. Fuska Ahmad ya haɗe sam babu alaman wasa akan fuskarsa haka ya juya ya nufi hanyar fita daga ɗakin, da kallo Saifuddeen ya bishi, wani ɗan guntun murmushi ya sake, haƙiƙa yasan Ahmad sam bayason aurensa da Zaleeha, ya kuma san dalili, amma yasan nanda wani lokaci kaɗan Ahamad ɗin zai fahimta. Cikin   zafin zuciya haɗi da fusata Ahmad ya nufi ɓangaren Ummi. Zaune Ummi take akan kujera gefenta kuwa Raliya ne zaune tana ta yabawa da koda d'inkunan zafafan laces ɗin dake gabanta, wanda Saifuddeen ne ya saya musu donyin fitan biki. Murya can ƙasan maƙoshi Ahmad yayi sallama, inda ya kutsa kansa cikin falon, fuskar Ummi cike da fara'a ta amsa masa, saidai kuma yanayin yanda taga fuskarsa yasanya taji ba daɗi, domin Ahmad mutum ne me yawan fara'a, baƙaramin abu bane zai sanya kaga ya ɓata fuska. Raliya kuwa ji tayi gabanta ya faɗi, sakamakon ganin mood ɗin mijin nata. Zama Ahmad yayi akan sofa tare da tanƙwashe ƙafafunsa. Dubansa Ummi tayi cikin sanyin murya haɗi da bayyanar da damuwarta tace. "Ahmad lafiya kuwa?." Ɗago idanunsa wanda sukayi jajur yayi ya kalli Ummin tare da miƙo mata wayar Saifuddeen dake hannunsa. Amsan wayar Ummi tayi tare da kai dubanta ga screen ɗin wayar, wanda har yanzu screen ɗin keda haske bai ɗauke ba, wanda shi Saifuddeen azatonsa Ahmad baisan security ɗinsa ba, shiyasama yabar Ahmad yatafi da wayan, shikuwa Ahmad dama tun tuni yasan securityn Saifuddeen ɗin, don ranan agabansa Saifuddeen yacire wayartasa a security. Idanu Ummi ta ƙurawa rubutun dake kan screen ɗin wayar, sannu ahankali take karanta saƙon, lokaci guda jikinta ya ɗauki wani irin rawa, take yanayin idanunta suka sauya daga farare zuwa ja,  aƙalla ta maimaita karanta saƙon yafi sau uku, batare da ta sani ba, sosai zafafan baƙaƙen maganganun da aka rubuta cikin saƙon ke yawo acikin brain ɗinta. Babu abun dayafi ɗaga mata hankali kamar inda Zaleehan ta rubuta cewa. ```"Ka turo iyayenka su janye batun aurena da kai! Su zo su kwashi wannan tarkacen da kasa aka tarkato aka kawo mana jidali. In kuma kaki yin hakan ka kuskura ka bari akayi auren nan aka kawoni mushen gidan kunnan to. Wallah Allah kenan``` Saifuddeen, in ka bari akayi auren nan cikin biyu za'ayi ɗaya ko in mutu ko ks matu!!!." Sosai tunanin Ummi ya tsaya cak, wani irin matsanancin tsorone ya daki zuciyarta, sosai kalaman Zaleeha suka ɗaga mata hankali, tabbas tanayiwa ɗanta Saifuddeen tsantsar so, bakuma tason wani abu da zai cutar dashi,  tayaya ma amatsayinta na Uwa zata zuba idanu tana kallo ɗanta yakai kansa ga inda ake neman halakasa, tabbas acikin kalaman na Zaleeha tagano cewa bata ƙaunar Saifuddeen ko kaɗan,  sam bazata taɓa bari Saifuddeen ya auri macen da take da bushashshen zuciya ba. Hawayen da suka cika idanunta tasoma ƙoƙarin shanyewa, cikin raunin daya bayyana akan fuskarta ta dubi Ahmad. Shi ɗinma Ahmad dubanta yayi, cikin rauni yace. "Ina takaicin tsananin son da Saifuddeen kewa Zaleeha, bata sonshi Ummi sam bata ƙaunarsa, bata ganin ƙima da darajarsa, tun awaje tana faɗa masa mugayen kalamai irin wannan inaga kuma idan anyi auren? ba fata nake ba Ummi amma sam banason abun dazai wargaza mana farin cikin mu, Saifuddeen kamar jigo yake agaremu baki ɗaya, bazan iya zuba idanuna naga ya jefa kansa cikin mawuyacin hali ba, Ummi zuciyar Zaleeha tayi zurfi sosai wajen tsanar Saifuddeen, saboda haka zata iyayin komai idan ya aureta." Ɗan tsagaitawa da maganan yayi tare da maida ƙwallan da suka cika idanunsa, ci gaba yayi da cewa. "Ai Nakasa Ba hauka bace bare tace baida hankali bazata iya zama da shiba, kuma Nakasar Saifuddeen bashi yake nuna cewa ya kasa ba,   mene aibun Saifuddeen Ummi? shin laifine don Allah Ya jarrabeshi da nakasa? ko kuwa laifine don yazamo kurma kuma gurgu, shi nakasashshe ba mutum bane kenan? Wallahi Ummi Saifuddeen bai dace da Zaleeha ba, saboda bata yarda da ƙaddara ba, hartanajin cewa ita watace, wacce ajinta ya ɗara nakasashshe, ta manta cewa da me lafiya da kuma nakasashshe duk halittar Allah Ne." Ajiyar zuciya Ummi ta sauƙe tare da sakin wani murmushi wanda yafi kuka ciwo. Cikin tsananin tausayin ɗannata Saifuddeen da irin ƙaddaran da Allah Ya ɗauro masa tace. "Inajin tsoro Ahmad, Inajin tsoron abun da zai faru nan gaba, bana fatan yarinyarnan  Zaleeha ta cutarmin Saifuddeen cutarwa mafi muni." Still ajiyar zuciya ta kuma sauƙewa, tare da miƙewa tsaye,  duban Ahmad takumayi cikin sanyin murya tace. "Ahmad zanyi abun da ya dace, abunda  kowacce uwa zatayi dan kare rai da lafiyar danta zanyi abinda ya kamata ace  tayi a matsayina na uwa!." Tana gama fad'in haka ta juya ta nufi hanyar ɗakinta. Tuni hawaye sun wanke fuskan Raliya, duk da cewa bata karanta saƙon da Zaleehan ta turowa Saifuddeen ba amma tabbas ta fahimci duk abun dake faruwa, daga cikin kalaman na Ummi da kuma mijinta Ahmad. Dubanta Ahmad yayi, itama kallonsa take, yayinda hawaye ke tsiyaya daga cikin idanunta, shin menene aibun Hamman'ta don yakasance gurgu kuma kurma? shima mutum ne kuma Namiji kamar kowa, yana da cikakkiyar lafiyansa na ɗa namiji, sannan gurguntan sa bazai zama kasawa agareshi ba, don meyasa Zaleeha zata ƙisa? Kai Ahmad ya girgizawa Raliya alaman ta daina kuka. Kasa jurewa tayi, hakan yasa ta faɗa cikin jikinsa tare da sakin kuka mai sauti. Rungumeta yayi ƙam tare da sake jawota jikinsa,  nan yamiƙe tsaye tana ajikinsa suka nufi hanyar barin falon. Suna fita suka yi karo da Hayatuddeen wanda shigowarsa cikin gidan kenan, sanye yake da white t shirt da kuma 3 guater jeans, hannunsa riƙe da wayarsa ƙiran Samsung yayinda kunnensa ke saƙale da earpiece,  yana ganinsu yaɗan yi turus tare da turo bakinsa gaba, har acikin ransa shikam yagaji da ganin Yayar tasa Raliya da Ahmad manne da juna sunashan soyayyarsu kamar tattabaru, kullum haka yake ganinsu liƙe da juna kamar wasu tif da taya. Hararansa Raliya tayi da jajayen idanunta,  sake kwaɓe fuska yayi yana shirin yi musu halinnasa na shagwaɓa ne, Ahmad ya miƙo masa wayar Saifuddeen, batare da Ahmad ɗin yace komai ba yaja Raliya suka nufi ɓangarensu. Da kallo Hayatuddeen ya bisu har suka ɓacewa ganinsa,  bakinsa ya taɓe ƙasa-ƙasa yace. "Hegu fitinanu, kuyi dai nima dana ƙara girma, ai dai zanyi auren nan ehe, don haka duk wani me ɗagamin kafaɗa ma gwara ya daina, nima ai zanyi auren bawai ba zanyi ba." Haka ya nufi ɓangaren na Saifuddeen yanata ƙunƙuni aransa. Koda ya ƙarasa part ɗin a parlour ya had'u da Salisu dake saurin fita, dan sunyi mgna da Saifuddeen kam batun Rashida na son su kai musu kud'in walima, so shine ya fita da sauri dan kai mata kud'in, cikin girmamawa yace. "Ina kwana Ya Salisu." "Lafiya lau Auta ya sakalci." Salisu ya amsa mishi ba tare da ya tsaya ba, Murmushi Hayatuddeen yayi tare da cewa. "Manyan angwaye sai b'are-b'are suke uwa hanji a langa." yana musu tsiya ya wuce ya nufi bedroom d'in Hamma Saifuddeen din nashi zaune ya sameshi akan wheelchair ɗinsa, inda ya tasa laptop ɗinsa agaba ƙiran company'n apple yana dannawa. Akan cinyar Saifuddeen ɗin ya ɗaura wayar tare da yin super ya faɗa kan lallausan gadon na Saifuddeen, lumshe idanu yayi yana me shaƙan daddaɗan ƙamshin na Hammansa, aransa yana fata ace watarana shima yazama kamar hamman nasa. Saifuddeen kuwa murmushi kawai yayi tare da ɗaukan wayar tasa ya duba, ganin still akan message ɗin Zaleeha yake, yasanyashi sakin murmushi, domin jikinsa ya basa cewa Ahmad bai cire wayan a security ba balle yayi amfani dashi. Cigaba yayi da aikinsa,yayinda time to time yake sipping exotic juice ɗin dake gefensa. A wunin ranan masu gyarannan suka gama komai na side d'insu Saifuddeen kafin azahar sun gama komai na side d'in masu buga kitchen cabinets ma sunzo sun shirya komai ras. masu fenti kuwa sun fento ko ina na gidan luggu da sak'o da yake sunada yawa kuma akwai kayan aiki kafin magrib dai sun gama komai gidan ya zama sabo fil yayi ras sai shek'i yakeyi da k'amshin sabon fenti. In da akayiwa gidan fentin Coral color iya rabi daga k'asa kuma dama tayis ne manne royal color hakan yayi masifar kyau ya haska gidan, cikin gidan kuwa Side d'in Ummi pumpkin color akasa daga saman pop d'in daga k'asa kuma navy blue mai shek'i, hakama saman inda Hayatuddee yake, inda Saifuddeen yake kuwa ba'a tab'abashi ba dan bai jimaba, Sai inda Raliya take mai mak'otaka da inda za'a ake shirin sa Zaleeha, mint green and white akayi mata komai yayi ras, sai wojen part d'in duka da aka fente da dark brown and daga d'an k'asan kuma tayis ne manne a jikin ginin, sai farfajiyar wurin da yakeda d'an zagayeyyen ma dai-daicin lambun da yakeda yabanyar grass carpet wanda yayi kore shar, sai bishiyar mangoro mai fad'i da tsananin duhu wanda yake baje kan bishi yoyin dabino da ayaba da gwaiba dake gefenshi dan bishiyar mangoron bata da tsawo sosai, a k'asan kuwa fulawowi ne jere wanda sune suka zama garkuwan wurin sai ya zama in kana cikin wurin baza'a hangoka ba, cikin wurin kuwa sai wasu fulawi masu halittar tim-tim in ka gansu kamar kujeru, kana ga kan pompoms guda biyu wanda dasu akeyiwa wurin ban ruwa, daga tsakiya ciluk kuma wani k'arfe ne mai tsawo wanda yake manne da fitilar sola mai d'an karen haske. sai irin kujerun silver nan da ake ajewa a asibitoci da wuraren shak'atawa, kujerun ne suka zageye wurin da k'asanshi ke wadace da koriyar ciyawar, ga sanyin tsirrai gana ruwan dake gudana a wurin ga na inuwar bishiyar mangoro dana dabino da gwaiba, uwa uba ga sanyin bishiyoyin ayaba kusan guda biyar da suka zagaye wurin, daga cikin wojen wurin kuwa an lailayeshi da intalak, sai babban baranda mai fadin da aka laileyeshi da tayis fari k'al. kana cikin parlour kuwa yasha fenti purple and cerise color sosai parlour yayi kyau hakama cikin two bedroom d'innan, kitchen d'inta kuwa an k'awatashi da durowowi masu kalar pink and white sosai aka k'awata kitchen d'in. komai fa yayi ras sai shek'i da k'amshi gidan keyi, hakama fulawin gidan duk anbi an musu sassariya an dai-dai tasu, garden dake bayan part d'in Ummi ma an gyarashi sosai, gida dai ko yanzu amarya tazo... Juyi take tayi akan makeken gadon nata,  gaba ɗaya damuwa ya cika zuciyarta, wani irin zafi takeji acikin ƙirjinta,  rumtse idanunta tayi, take wasu irin hawaye masu zafi suka kwaranyo daga cikin idanunta, ya zatayi? wazata kaiwa kukanta ya share mata hawaye?  burinta shine koda mutum ɗaya ne ya fahimceta, amma ankasa samun hakan,  sosai zuwa yanzu ƴan uwanta keyi mata kallon wanda aljanu suka kama,  laɓɓanta ta ciza tare da sakin wani marayan kuka mai sauti, ta lura shi wannan nakasashen jikinshine a nakasashe zuciyarsa cike take da jarumta, dan ta fahimci duk baraza da ihu da hargowar da take mishi akan ransa da rayuwarshi a banza, babu alamun karaya bare fargaba ko d'igon tsoro, asalima sai tsoronshi dake cika mata idanu muddin ta kalli kwayar idanunshi koda na one second ne. Juyi ta kumayi tare taune lip d'inta na k'asa ayanzu tafi buƙatarsa fiye da dacan baya, fatanta burinta, muradinta duk sun ta al'laƙane akansa, sam soyayya batayi mata adalci ba da ta jefata cikin mawuyacin hali,  hannunta ta sanya ta dafe dai-dai saitin zuciyarta dake bugawa, tanajin sonsa na fusgarta, wani irin maganaɗisun ƙaunarsane ke ƙara janta akowacce rana,   yaya zatayi da soyayyarsa dake ƙoƙarin fasa mata zuciya? Ƙaddara tazo mata ayanda bata taɓa zata ba, ƙaddara ta zautar mata da tunani, har takai ga tanayin komai cikin zaucewar hankali. Sosai tayi hugging pillow, ahankali taci gaba da rera kukanta, saida tayi kuka sosai kafun wani wahalallen bacci ya ɗauketa. Washe gari. Zaune suke su dukansu akan babban dinning table ɗin dake  cikin falon, Saifuddeen, Hayatuddeen da kuma Raliya, sai Ahmad wanda shigowarsa cikin falon kenan. Ahankali Saifuddeen ke tsakalan abincin yana kaiwa bakinsa,  gaba ɗaya hankalinsa naga wayarsa dake riƙe ahannunsa, sosai yashiga busy tunda aka fara shirye-shiryen bikin, dan ma yanada tarin aminai dake ji da komai wani abinma sai dai kawai yaga anyi sosai suke shiryawa bikin inda ya kama yau saura kwana uku bikin. Tunani yakeyi akan tirelar dake can harabar gidan nasu wanda aka kawo kayan Zaleeha. Tirelan cike yake dam da kayan Zaleeha wanda Ya Ahmad yayi mata komai na duniya wanda amare zasu buk'ata. Wanda Habu ya bada shawaran kada a sauk'e kayan a gidansu a wuce dashi gidan Saifuddeen d'in acewarsa k'arin jidaline. to koda ya gayawa Ahmad sai suka bawa driver'n tirelar hak'uri akan zasu biyashi abar kayan a ciki sai an gama gyaran side d'in amaryar sai su sauk'e kayan to su kuwa jin za'a biyasu yasa suka amince. to an gama gyara a bisa tsarinsu dai gobe za'a zo a sauk'e kayan sannan tuni Salisu ya nemi masu had'a kayan su shirya za'a biyasu dubu saba'in kud'in aikinsu kana Maryam da Aunty Lubna zasu zo su kimtsa komai duk a goben... Ummice ta ƙaraso cikin falon, cikin shirinta tsab, sosai tasha ado irin wanda ya bayyana cikar kamalarta, tana ƙarasowa cikin falon gaba ɗaya kallon ƴaƴan nata ya dawo gareta. Ahankali Saifuddeen ya ɗago da kansa ya kalli Ummin nasa, ganin yanda tayi masa kyau yasanyashi sakin murmushi, tare dayi mata duban tsab, domin yaga alaman cewa fita zatayi. Ƙarasowa dinning area'n Ummi tayi, hannu tasanya ta shafa kan autanta Hayatuddeen dake ta faman zuba wa cikinsa, spiring roll. Fuska Saifuddeen ya kwaɓe tare da karyar da wuyansa gefe, Matsanancin tausayinsa ne ya cika zuciyar Ummin, don sarai ta fuskanci abun da yake nufi, alamune dake nuni yanada yar damuwa can k'asan zuciyarshi wanda kuma baya son ta sani, ita kuwa in taga hakan bata matsa mishi kan ya sanar mata sai dai takanyi k'ok'arin sashi farin ciki, sai dai tasan yanzu koma menene aransa baya rasa nasaba da Zaleeha, hannu tasa ta shafa kansa shima. Murmushi yayi inda cikin body language ɗinsa yayi mata alaman da ina zataje. Itama murmushin tayi tare da gyara tsayuwarta, duban ƴaƴan nata tayi dukansu, tare dayi musu bayani akan zuwanta Dukku da ta tsarashi yau da safe, sannan kuma ayau ɗin zata dawo, sosai suka ɗanyi mamaki sai-dai kuma sanin cewa ana tsaka da shirye-shiryen hidiman biki ne yasanya basu damu ba, don atunaninsu wani uzurine wanda ya shafi bikin zai kaita Dukkun. Haka Ummi tayi sallama da su, inda dukansu suka rakota har compound ɗin gidan. Saida suka ga tafiyarta kafun su dukansu suka koma cikin gida. Kusan ƙarfe shabiyu da wasu ƴan mintuna Ummi suka iso cikin garin na Dukku me al'barka. Kaitsaye gidan Bappa Ali suka sauƙa. Sosai Aunty Mina tayi murnar ganin Ummin, nanfa lokaci ɗaya tacika mata gabanta da kayan ciye ciye, hadda dangin su fura da nono, Sosai Ummi da Auntyn ke shan hiransu, kasancewar Bappa Alin bayanan, sunje gaisuwan wani abokinsu wanda bashida lafiya, shida Malam Ashiru. Cikin ikon Allah Kuwa Ummi na idar da sallan azahar saiga Baffa Alin ya shigo, koda yaga Ummin yaji daɗi, saidai kuma zuciyarsa ta basa kan cewa ba lafiya ba, domin lafiya ƙalau babu abun da zaikawo Ummi Dukku ana tsaka da shirye shiryen bikin Saifuddeen kana kuma jiya-jiya nan sukaje amsa kiran nata. Bayan sun gaisa da Bappa Alin ne Ummi ta gyara zama, lokaci ɗaya damuwa ya bayyana akan fuskarta, dubanta Baffa Ali yayi cikin sanyin murya yace. "Lafiya kuwa? badai wanine bashida lafiya acikin gidan ba?." Kai Ummi ta girgiza cikin ƙunan zuciya tace. "Akan maganan auren Saifuddeen da yarinyar nanne, kamar yanda na faɗa muku kaida Malam Ashiru jiya cewa yarinyar nan batason Saifuddeen, tana masa barazanar matuƙar ya aureta zata kasheshi, to fa yanzu abin k'aruwa yakeyi dan bata daina ba, awancan karon kun tausasheni ta hanyar cewa nayi haƙuri nabari ayi auren, na haƙura badon raina yana soba, saidai ayanzu bazan iya haƙura ba, inamatuƙar jin tsoron abun da zai faru anan gaba, inatsoron rasa Saifuddeen, Bappa Ali kasan yanda Saifuddeen yake awojenmu dan Allah Kayi wani abu!." Nan ta kwashe duk kan abun daya faru da kuma text message ɗin da ta karanta wanda Zaleehan ta turowa Saifuddeen ta faɗa masa. Ajiyar zuciya maiƙarfi Bappa Ali yayi, tare da sanya hannu ya ɗan dafe kansa, tabbas zuwa yanzu yakamata yabita maganan Ummi, don kuwa tabbas ayanda Zaleehan ke faɗa da kuma bayyana tsanar Saifuddeen afili tabbas zata iya aikata koma miyene don ganin ta cutar dashi, tabbas shima zuwa yanzu kam yafara tsorata da al'amarin. Ɗan jim yayi tare da gyara zamansa, cikin kulawa yace. "Insha Allahu Ayau yau ɗinnan zan ɗauki Malam Ashiru mu tafi Gombe tun lokaci bai ƙure mana ba, haƙiƙa wannan lamari yayi tsaurin da dole sai manya sun shiga cikinsa, ki kwantar da hankalinki, Insha Allah zamuje mu samu shi Malam ɗin, zamuyi magana ta fahimta dashi, bakuma zamu ɓoye masa komai dake faruwa ba, tabbas nasan zai fahimce mu, shi kuma Saifuddeen Allah yabasa wata mace tagari wacce ke ƙaunarsa!." Ajiyar zuciya mai ƙarfi Ummi ta sauƙe tare da cewa "Ameen!." Har cikin ranta taɗanji sanyi, haka dai suka ɗan taɓa hira kaɗan kafun daga bisani tace zata koma. Haka suka rakota har wajen mota inda Sule driver ke jiranta. Haka Ummi suka kama hanyar shigowa cikin garin Gombe zuciyarta wasai, tanajin kamar ta raba Saifuddeen da ƙaya. Tafiyar 1 hour ne kacal ya kawosu Gombe, inda ta koma gida zuciyarta cike da salama, saidai kuma ta wani ɓangare, cike take da tausayin Saifuddeen, domin kuwa koda sau goma zata kalleshi, to akowani kallo ɗaya, saita hango zazzafar ƙaunar da yakeyiwa Zaleeha acikin ƙwayan idanunsa. Amma addu'a bata bar komai ba. Zata tayi masa addu'a akan Allah Ya musanya masa da mafi alkhairi. Su Bappa Ali kuwa ƙarfe biyar dai-dai suka kamo hanyan zuwa garin Gombe shida Malam Ashiru, daga cikin abun da Ummi ta faɗa masa, ko ɗaya bai rage ba, haka ya labartawa Malam Ashiru komai, shikansa Malam Ashiru saida yaji zuciyarsa tayi masa ba daɗi, tabbas yasan sharrin ƙiyayya, ƙiyayya bata da daɗi sam, kuma takan rufewa mutum ido, yayi duk abun dayaga dama, musamman ma ga mace da auren mijin da bata so dan haka shima ya yarda baza'ayi wannan aurenba. Ƙiran sallan Magriba acikin garin Gombe tayi musu, nan suka tsaya sukayi sallah, inda suna idarwa suka nufi gidan Dirankaɗi, wato Baban Ishaq kenan, kasancewar tunkan su taso sunyi masa bayanin komai sun kuma sanar dashi zuwansu, inda shikuma ya ƙira Baba Malam ya shaida masa cewa da anyi sallan Isha za su zo. Koda suka ƙarasa gidan na Dirankaɗi, anan sukayi sallan Isha, daganan suka wuce zuwa G.R.A wato unguwar su Zaleeha. Tarba me kyau suka samu daga Baba Malam, inda ya sauƙesu acikin babban falonsa, nan yasa aka cika musu gabansu da kayan ciye ciye, hira kaɗan suka ɗan taɓa, kafun Dirankaɗi ya gyara zama inda ya fuskanci Baba Malam, cikin nutsuwa haɗi da halin dattako yashiga labartawa Baba Malam abun dake faruwa, da irin saƙon text message din da Zaleehan ke turawa Saifuddeen wanda suke ɗauke da barazana haɗi da baƙaƙen maganganu, inda ya ɗora da cewa. "Kayi haƙuri Malam, amatsayinmu na manya masu hankali, baikamata ace mun zuba ido hakan na faruwa ba, haƙiƙa duk auren da akace akwai ƙiyayya acikinsa to mafi al'khairi shine barinsa, tabbas babu wani uba dazai so ɗansa ya rasa iri awannan gida naka mai cike da kamala haɗi da tarbiya, saidai kuma babu yanda zamuyi ɗaukan ƙaddara ya zame mana dole, saboda hakane mukazo baka haƙuri, kayi haƙuri Malam bisa dole munjanye nemawa Saifuddeen auren Zaleeha da mukayi, fatanmu shine Allah ya bawa kowannensu abokan zama nagari!." Ajiyar zuciya Baba Malam ya sauƙe tare da ɗanyin jigum, tabbas Zaleeha nason dasa masa ciwon zuciya, sannan tanason zubar masa da ƙima da kuma mutumcinsa a idanun jama'a, saidai kuma yayi al'ƙawarin bazai taɓa bari hakan ya faru ba, gyara zamansa yayi tare da duban su Baffa Ali, cikin dattako haɗi da tausasa zance yace. "Babu wani abu dazan faɗa muku face haƙuri, kuyi haƙuri, haƙiƙa nine nan mahaifin Zaleeha, sannan nike da ikon bada aurenta ga koma waye, tuntuni nakuma bada aurenta ga Saifuddeen, kamar yanda Zaleeha take ƴa awajena, hakama Saifuddeen, shi ba iya ɗalibina bane kaɗai, inajinsa kamar jinina, saboda haka kuyi haƙuri, kujanye batunkun fasa auren, Zaleeha ƴatace kuma inada ikon tanƙwarata duk yanda naga dama, kuyi haƙuri ku ɗauka cewa duk waƴannan abubuwan da takeyi yarinta ne kuma zata daina watarana, tabbas nasan yanzu giyar ƙuruciya ne ke ɗibanta, nan gaba kaɗan bazatayi abun da tayi yanzu ba." Ɗan jim yayi tare da cigaba da cewa. "Kuyi haƙuri dan Allah, Amatsayina na Uba agareta na baku haƙuri, kuma kamar yanda kuke sha'awar haɗa zuri'a dani, haka nima nake sha'awar haɗa zuri'a daku, musamman Saifuddeen daba kowani uba bane zaiƙi son zamowarsa suruki agaresa, kamar yanda na faɗa muku tun daga farko babu abun da zan faɗa daya wuce nace kuyi haƙuri insha Allah aurennan ba fashi." Da sauri Malam Ashiru ya fara jujjuya kai a hankali tare da cewa. "A a Malam kayi hak'uri abar batun auren nan mu kam mun janye.....! BY *GARKUWAR FULANI* [9/9, 9:05 PM] +234 806 222 4030: Ahankali ta murɗa ƙofar toilet ɗin ta fito,  sanye take da wani pink ɗin bathrube yayinda gaba ɗaya gashin kanta ke jiƙe da ruwa, da dukkan alama dai, daga wanka take,  fuskarnan tata akwaɓe take sam babu alaman fara'a asamanta, sosai abunda Saifuddeen ɗin yayi mata safiyar jiya yake cinnta tare da ƙara sosa ranta, inda yake ƙara motsa duk wani ɓacin ranta,    ƙarasawa gaban dressing mirror tayi ta zauna, dai-dai lokacin aka turo ƙofar ɗakin aka shigo,  azabure ta juyo don ganin kowaye yayi gangancin shigo mata ɗaki babu sallama. Idanunta ne sukayi mata tozali da Balkeesu, ganin Balkeesu yasa ta sauƙe ajiyar zuciya, tare da juyawa tasoma ƙoƙarin shafa mai ajikinta, don acikin yanayin ɓacin ran da take ciki batajin zata wani iya nunawa Balkeesun cewa tayi farinciki da zuwanta. Cikin yanayi na tsantsar mamaki Balkeesu ke kallon Zalihan, ba abun daya ɗaga hankalinta kamar ganin gashin Zaleehan ajiƙe da tayi, cikin mamaki haɗi da tsantsar gulma dake cinta tace. "Zaleeha badai barinsa kikayi yayi ba?." Juyowa Zaleeha tayi tare da ɗan dubanta, cikin rashin fahimtan maganan Balkeesun fuska a haɗe tace. "Yayi me?." Hararanta Balkeesu tayi tare da cewa. "Meyasamu gashinki naganshi ajiƙe? inafatan ba kanki kika mallaka masa ba dai ko?." Wani irin harara Zaleeha ta bankawa Balkeesu, tare dayi mata kallo, irin na baki da hankali ɗinnan. Cikin hasala ta furzar da iskan bakinta, inda tace "Allah ya sauwaƙe ni Zaleeha nabawa wani wanda ba zaɓin raina ba jikina,  ke koda ma zan iya mallakawa wani kaina, to kidaina tunanin zan mallakawa wannan mugun virginty ɗina. To wai ma kina tunanin ayanda yake always akan wheelchair zai iya amsan virgin ɗin macene, chab shirme ma kenan, mutumin da kullum yake bisa kujera kamar wani sarki."  taƙare maganan tana me taɓe bakinta. Murmushin jin daɗi Balkeesu tayi tare da cewa. "Nasani ko zai iya karɓa abu a duhu." Tsuka Zaleeha tayi tare da cigaba da shafa body lotion ɗinta. Tana kammalawa taɗan murza powder akan baby face ɗinta,  tashi tayi tare da ƙarasawa gaban makeken drawer ɗinta,  wani yadi mai laushi wanda yaji ɗinkin riga da sket ta ciro tare da sanyawa, sosai kayan yayi masifar amsar jikinta, sosai surar jikinta ya bayyana, musamman ma hips ɗinta, dogon gashinta ya kama atsakiyar kanta, inda tayiwa kanta wanka da wani turaren oud mai ƙamshin gaske. Duk abun nan da takeyi idanun Balkeesu na kanta, sosai Zaleehan tayi mata kyau,  tarasa meyasa hakanan Zaleeha kowani kaya tasa sai sunyi mata kyau, wannan yana ɗaya daga cikin abun da yasa, akullum kishin Zaleehan ke ƙara ruruwa acikin ranta, akusa da ita Zaleeha ta zauna tare da dubanta, cikin takaicin abun daya faru jiya tsakaninsu da Saifuddeen ɗin tace. "Bazan zauna ba Balkeesu, inajin kamar ana huramin wuta aƙasan zuciyata, sam bazan iya cigaba da zama agidannan ba, wlh ji nake kamar ana korata daga ɗakin, akullum tsanarsa ƙara yawa take acikin zuciyata, banajin zan zauna har zuwa lokacin da muka tsara in sashi ya sakenin, idan ban gudu yauba to tabbas zan gudu gobe." Murmshin gefen baki Balkeesu tayi, take zuciyarta tayi haske, dajin maganganun Zaleehan saitaji kaman an ɗauke mata wani nauyi dake kan ƙahon zuciyarta ne. Gyara zama tayi tare da duban Zaleehan cikin ƙara ƙarfafa mata taurin zuciya tace. "Bazan ce kada ki gudu yau ko gobe ba Zaleeha, saidai kuma guduwarki da gaggawa, zai iya haifar da rugujewar plant ɗinmu, tunda ai in guduwa kikayi da aurensa a kanki zaki gudu ko, ni kuma nafi son ki sashi ya sakeki inma zaki gudun kinga kin fita rayuwarsa salim alim, sannan kadafa ki manta da cewar shekaran jiyannan aka kawoki, kibar maganan guduwan nan har sai lokacin da muka tsara ya cika please ki tsurfa musu rashi mitunci gidan gaba ɗaya ta yadda dole ya sakeki." Kai Zaleeha ta rinƙa jujjuya mata cikin sanyin sauti tace. "Bazan iyaba, me mutanen gidan sukayi min da zan musu rashin ɗa'a? Ina son Umminshi dan tanada kirki hakama ƙannenshi suna sona, kuma nima ina sonsu musamman Ummi da autanta, Kuma shima ɗin ya za'ayi in mishi rashin kunyar bayan tsoronshi nakeji yanada kwarjini da yawa, ko idanunshi bana iya jurar gani, kuma dai ko yaya zanyi yanzu yana matsayin mijina ne, ya zanyi mishi tijara Allah yayi fushi dani in tarawa kaina zunubi. Gwara kawai in gudu yafi min al'khairi, bazan iya zaman ɗakin nanba da gidan Allah ji nake kamar korata akeyi." Wani irin mugun harara Bilkeesu ta watsa mata kana tace. "To mai imani da miji da tsoron Allah ai sai ki gudun kifi ruwa gudu in kinga dama ki dai sani in kin gudun nema tofa da aurenshi a kanki." Shiru Zaleeha tayi tare da kawar da kanta gefe, tarantse bazata zauna da Saifuddeen ba, tagwanmace ta tabbata babu aure datai ta zauna dashi, tana ji a jikinta da zuciyarta cewa zata jira abun sonta, koda nan da shekara ɗari ne,  sam zama da Saifudden banata bane. Saifuddeen kuwa, hakanan yakejin zuciyarsa wasai tun jiyan,   sosai murmushi ke bayyana akan kyakkyawar fuskarsa, musamman ma idan ya tuna da mood ɗin Zaleehan na jiyan tsantsar tsoronshi ne da fargaba ya hango acikin ƙwayan idanunta can ƙasan tsiwar da take mishi,  kaitsaye banɗakinsa ya wuce,  wanka yayi sannan yafito inda ya kimtsa kansa cikin wata ɗanyar purpule ɗin shadda mai masifar kyau, sosai yayi kyau, yayinda farar fatarsa taƙara bayyana acikin kayan,  shaddan irin ɗinkin nan na half jumper akayi mata,kasancewar haka nan shiyake bayason full jumper yafison half, duba da yanayinsa wanda ko yaushe azaune yake, so bayason duk wani abu dazai takurasa. turarensa mai daɗin ƙamshi ya fesa, tare da sanya Cumb yaƙara taje kwantacciyar suman dake kansa, ƙarasawa gaban mirror yayi tare da ɗan duban kansa, shikansa yasan cewa yayi kyau, cikin nutsuwa ya danna madannin kekensa, wayoyinsa kawai ya ɗauka, inda ya fice daga cikin ɗakin, koda yazo falon na Zaleeha bai iske kowa cikinsa ba, hakan yasa kaitsaye yafice daga sashin nasu. Direct ɓangaren Umminsa ya nufa, tundaga bakin ƙofar falon na Ummi yakejin hayaniya na tashi, koda ya shiga nan ya iske su, Ahmad, Ishaq, Wareesu, Saminu da kuma Saleesu, Mudassir harma da Hisham da Jabeer, Aziz gaba ɗayansu sun baje, yayinda aka cika musu gabansu da kayan ciye ciye, Ahmad da Salisu ba kunya haka suke lodawa cikinsu abinci, sam baruwansu da wani surkuntaka, saboda sunaganin duk suɗin ƴan uwan junane, haka kuma Ummi mahaifiyace agaresu, saboda haka babu wani batun noƙe-noƙe, duk da cewar ansan fulani da kunya, saidai sabo da kuma zumuncin dake tsakaninsu ya goge wannan kunyan. Cikin mamaki yake kallonsu don sam basu sanar dashi zuwansu ba. Ƙarasowa cikin falon yayi,  inda yakai hannu ya zunguri Ishaq wanda ke  ta faman suɗe hannunsa wanda yaci masa dashi, bakomai yasashi suɗe hannunba kuwa face daɗin miyar masan, shikam har yau baiga macen da takai Ummin Saifuddeen iya girki ba. Ishaq kuwa cikin gane wanda ya zungureshi yace. "Banason wulaƙanci fa Saifuddeen, wato wulaƙanci zaka mana saboda mun riga mun damƙa maka amaryarka a hannunka ko?." Gaba ɗayansu sukayi murmushi inda Saminu yace. "Manta dashi da Allah, nasan bazai wuce haushinmu yakeji ba, kasan dai Saifuddeen sakaline baison wani ya raɓi masa Umminsa, kuma mumadai Ummin nan nasonmu." Saminu yaƙare maganar yana me kai loman gandar fatan saniya, wanda yaji haɗi sosai, sai ƙamshin su kanumfari yake. Kai Ahmad ya girgiza tare da duban Saminu cikin yanayi na tsokana yace. "Surkinka nefa Yayan matarka." Hararansa Saminu yayi tare da cewa. "Kamanta tare mukai wasan ƙasa." Dukansu suka saka dariya, banda Saifuddeen wanda shi kullum murmushine aikinsa, da haka yasaba kuma hakan yafi yi masa kyau, aduk sanda yayi murmushi idan kumatunsa da tsakiyar gemunshi da goshinsa suka lotsa, sai yayi wani irin fitinannen kyau. Dai-dai lokacin Ummi da Goggo Dada suka fito daga cikin kitchine, bayansu kuwa Raliya ce riƙe da plate, wanda samansa ke shaƙe da yankakkun kayan fruits, agabansu ta dire musu plate ɗin, duban Ummi Saifuddeen yayi tare da shagwaɓe fuskarsa, cikin body language ɗinsa yayi mata alama da cewa. "Shine kika wahalar da kanki wajen haɗawa waƴannan ƙattin abun karin kumallo ko bayan ga matansu!." Gane abunda yake nufi yasanya Ummi sakin murmushi,  ƙarasowa cikin falon tayi tare da sanya hannu ta shafi lallausan suman kansa, cikin kulawa tace. "Ae duk al'barkacin aurenka sukeci." Jin abun da Ummin nasa tafaɗa yasanyashi sakin murmushi, idanunsa ya ɗan lumshe, ahankali ya dubi Goggo Dada nan yayi mata alamun gaisuwa, da fara'a ɗauke akan fuskarta ta amsa, tare da ƙarayi masa murnar biki. Nan suka zauna inda suka shiga ɗan taɓa hira kaɗan, su Hisham na gama kammala cin abincin Goggo Dada tasanar dasu cewa zasu buɗe kan ango da amarya tunda dai jiya bata samu taje wajen diner ɗinba,  nan dukansu sukayi na'am, inda Aunty Meenat ma da fitowarta daga ɗakin Ummi kenan tace itama zata yiwa ango nasa liƙin,  su Adda Rahama da Raihana ne suka firfito falon, nan fa Ummi tace da Raihana taje ta ƙirawo amarya. Zaleeha kuwa har zuwa yanzu suna tare da Balkeesu, inda Balkeesu ke ƙara fomfata tana kuma kunnata akan kada ta gudu ta tsaya ta fetsarewa mutanen gidan ta yadda uwarshi da kanta zatasa ya saketa shi kuma ta nuna kasheshi zatayi,  ita dai Zaleeha abun daya dameta ne ya isheta don wannan karon dai zugar bilkeesu ba abar ɗaukar mai hankali bane, to bare kuma asirin Mama ya riga zugar tasiri. Ƙoƙarin kwanciya take, sukajiyo knocking door,  azaton Zaleeha Zaheera dake kallo afalo ne hakan yasa tace. "Yes come in." Ahankali Raihana tatura ƙofar ɗakin tashiga, ganin Raihana yasa Zaleeha ɗan sakin fuskanta, duk da batasan wacece ita ba, amma kallo ɗaya tayi mata ta hango matsanancin kaman da sukeyi da Aljanin gurgun da tsanarsa tayi mata tsaye acikin rai sosai ta yaba da kyan Raihana kuma har ranta taji tana sonta. Balkeesu kuwa baki tasake tana ƙarewa Raihanan kallo, gaba ɗayama hankalinta yatafi ga tsadadden zanin dake jikin Raihana'n, domin kuwa babban Chiganvy ne ɗan ubansu. Murmushi Raihana tayi tare da duban Zaleeha cikin kulawa tace. "Idan babu damuwa muna buƙatarki afalo, za'a ɗanyi muku buɗan kai ne!." Dammm haka Zaleeha taji ƙirjinta ya doka, sam batason abun dazai ƙara haɗata dashi, musamman idan ta tuna da abun daya shiga tsakaninsu jiya saitaji kanta kamar zai buga gaba ɗaya tsoro lamarinshi ke bata. Cikin baƙinciki da takaici Balkeesu tace. "Mezai hanamu zuwa kuwa, ai zamuzo yanzun nan." tafaɗa tana me miƙewa tsaye dan samawa Zaleeha mayafi, ɗan murmushi Raihana tayi tare da cewa. "Badamuwa, ai bama sai kunzo ku dukanku ba, itaɗin dai kawai muke buƙata!." ta ƙarishe mgnar cikin yatsina fuska dan sam ita da Bilkeesu bata konta mataba, Zaleehan kanta a fakaice take sonta tunda ance bata son Hammanta ita kuwa duk wanda yace baison Hamma Saifuddeen ɗinta itama bazata sotaba. Ƙasake Balkeesu tayi tare da watsawa Raihana harara ƙasa-ƙasa, tabbas maganace afakaice Raihanan ta faɗa mata, amma dai koma menene ta rantse saitaje anyi buɗan kan da'ita. Wani tsantsareren mayafi laffaya Zaleeha ta yafa aduka jikinta inda ya sauƙo ya rufe har fuskarta, wani flat shoe kalan yadin jikinta ta sanya aƙafafunta,  Raihana da kanta taƙara fesa mata turare nan Balkeesu uwar gulma tariƙe Zaleehan, Raihana na gaba sukuma suna biye da ita abaya haka suka nufi cikin gidan. Sunanan zaune afalo suna ɗan taɓa hira, daddaɗan ƙamshin daya ziyarci hancinsa shiyafara sanar masa da zuwanta, juyawan dazaiyi kuwa ya hangota cikin wani light orrange ɗin mayafin laffaya mai tsananin kyaun gaske, sai walwali da sheƙi yake, Raihana da kanta ta kamo Zaleehan, inda ta zaunar da ita akan kujeran dake facing na Saifuddeen ɗin, tsulum Balkeesu daketa faman ƙarewa falon kallo tazo ta zauna akusa da ita, sosai Balkeesu tasha mamakin haɗuwan falon, wanda kuma yake mallakin Ummi, sam abubuwan mutanen suna shammatan ta, kwata-kwata bata taɓa tunanin yawan arzikinsu har yakai haka ba, duk abun da sukayi takan ɗauka, ƙaryane kawai da fafa, wani abun kuwa takanyi tunanin sunayinshi ne kawai don su mallaki Zaleehan, saidai kuma tunaninta ya fara sauyawa ne tun lokacin da aka kawo Zaleehan gidan,  yanzu kam tagama yarda cewa suɗin masu arziki ne, duba da irin kuɗin da aka kashe wajen ƙawatawa Ummin nasu falonta, uwa uba ga ƴan uwan Saifuddeen ɗin da ako yaushe suke cikin sutura mai kyau, da shiga ta al'farma domin kab cikinsu babu wacce take sanye da ƙasa da  kayan dubu ashirin, saima yayi sama, kowa kagani acikinsu masha Allah, Gaba ɗayansu cikin jindaɗi da rufin asiri suke rayuwarsu gasu kyawawane ajin forko, duban Adda Rahama wanda ke sanye da wani jan leshi mai shegen tsada tayi, taɓe baki tayi, cikin ranta tace "Ƴan iska, kowa kagani cikin farinciki yake, badai Saifuddeen shine farincikin ku ba, hmmm ai na gano lagonsa, rashin Zaleeha shine baƙin cikinsa, kukuma baƙin cikinsa shine tashin hankalinku, to kuwa kushiryawa tashin hankali, don wallahi al'ƙawari nayi sai nasa Zaleeha tasa ya saketa saki mafi muni kafin insata ta gudu daga gidannan."   ƙasa-ƙasa tayi ƙwafa, tare da cigaba da ƙare musu kallo. ita kuwa Zaleeha shiru tayi kanta a sunkuye ta cikin mayafin ta zubawa ƙafafun Saifuddeen ido, wanda suke ƙal-ƙal kana daga ganinsu zasuyi tsananin laushi da taushi kodan hakan bazai rasa nasaba da rashin takawarsuba daga ganin fatar tiɓis zatayishi laushi, yatsunshi ta zurawa ido tana kallonsu tamkar ka taɓasu jini ya tsallo kan faratun yatsun nashi ta maida idanunta ganinsu ƙal-ƙal yasata ɗan kauda idonta, a ranta take tajjudin yawan tsabta na wannan nakasasshen aljanin yakeda shi sabida ita fa tana alaƙanta kyan Saifuddeen da iska, takalmanshi dake gefe ta kalla wanda suke na Gucci a tsiwace cikin ranta tace, "Hmmmm gurgu kafi mai ƙafa iya shege, shi komai nashi mai tsada, wannan da lafiyarsa lau, alla'anɗi iya ƙasaitar da zai zuba. Shi kuwa Saifuddeen kota kanta baibiba hira yake da abokanshi. Bilkeesu kuwa sam bata tsinke da al'amarin nasu ba saida taga yanda Ummi da kuma Goggo Dada ke yiwa Saifuddeen ɗin ɓarin kuɗi, sosai suka zuba masa kuɗi, inda Aunty Meenat ma tazuba masa nata, nanfa kuma suka dawo kan Zaleeha,  Goggo Dada ne tasa Raliya ta buɗe mata mayafin, nanfa suka shiga zuba mata kuɗi itama, sosai suka zuba mata nairori, Ummi ne ta dubi Raliya inda tace taje ɗaki akwai wani gift da ta ajiye akan gado ta ɗauko mata, babu ɓata lokaci kuwa saiga Raliya ta dawo, hannunta ɗauke da wani ƙaton gift wanda aka masa ado da pink flowers, sosai yayi kyau, hannun Zaleeha Ummi takamo inda ta sanya mata babban gift ɗin cikin nutsuwa tace. "Wannan tukuici ne agareki na zamantowa matar ɗana da kikayi, Allah Ubangiji yayiwa rayuwar aurenku al'barka, sannan yabaku zuri'a ta gari tare da zaman lafiya mai ɗorewa." Gaba ɗaya jama'an wajen suka amsa da Ameen, saidai banda Zaleeha, sai kanta data sunkuyar alamun jin kunya, kana tanata wasa da yatsun hannunta. Sosai Ummi taji ƙaunar ƴarinyar a ranta komai da nitsuwa da kunya take yinshi. Balkeesu kuwa da ƙarfi tafaɗi Ameen ɗin, wanda hakan kuwa da biyu tayishi, sam bataso sugane cewa itaɗin munafukace, don tafuskanci cewa kamar, Raihana ta ganota. Haka suka gamayi musu buɗan kaiɗin cikin nuna ƙauna, Balkeesu ne tajata suka koma part ɗinta bayan duk an haɗa mata kuɗin. Su kuwa su Saifuddeen anan falon Ummin sukaci gaba da zama. Suna shiga cikin ɗaki, Balkeesu wanda jikinta ke mazari ta amshi gift ɗin, hannunta har rawa yake wajen ƙoƙarin buɗewa. Zaleeha kuwa mayafin dake jikinta ta yaye, cikin ƙunan zuciya tayi wurgi da mayafin, faɗawa kan gado tayi tare da lumshe idanunta, sam batajin tsanar kowa dake cikin gidan saishi kaɗai haka nan taji tana so duk mutanen gidan sabida ta lura sunada karamci da mutunci kuma sunfi ƙarfi tijara koda da ƙwayar zarrane a wurinta. Ihun da Balkeesu tayi shiyasanya Zaleehan ɗagowa da sauri ta dubi Balkeesun, cikin yanayin mamaki haɗi da firgita Balkeesu tace. "Gold, Zaleeha Gold ne fa aciki da kuma turaruka masu tsada ga kuɗin duk ke akabarwa." Wani haɗaɗɗen kwalban turare Balkeesun ta zaro tare da cewa. "Zaleeha kinkuwa san kuɗin wannan turaren?, oh my God ashe waƴannan mutanen masu kuɗine sosai har haka!!." Wani dan ƙareren agogo da sarƙan gold Balkeesun ta ciro, wanda aka ƙawata gidansu da wani farin glass, cike da mamaki tace. "Lallai kuwa mutanen nan sunshiryawa auren nan, what a surprise."  Kallon sarƙa da agogon Zaleeha tayi, wanda lokaci ɗaya sukayi bala'in yi mata kyau, amma ayanda takejin zuciyarta yasa bata  nuna ba, maida kanta jikin pillow kawai tayi tare da lumshe idanunta, abun daya dameta shine aranta ita kuɗinsu baya gabanta. Balkeesu kuwa kaman Zararriya haka ta dinga yaba kayan, saida tagaji don kanta sannan tayi shiru, nan kumafa zuciyar hassadan nata ta motsa, take taji wani danƙareren baƙin ciki ya cika zuciyarta, inama da ace itace tasamu wannan kayan more rayuwa haka? wai ma shin maiyasa ita rayuwa bata zuwar mata da garaɓasa haka? lallaima dole ne taraba Zaleeha da wannan gidan, idan bahaka ba tanaji tanagani zasu maida Zaleeha millionaire girl, ita tananan zaune Zaleeha zata shiga cikin sahun manyan mata, wanda kokaɗan kuwa ita bata fatan haka, dole ne ma taƙara zuga Zaleeha akan batun a sakin kafin guduwarta, don kuwa ayau ɗin ta hango irin tsananin soyayyar da dangin Saifuddeen ɗin keyi masa, tabbas ayanda tafahimta ayanda suke masifar sonsa, to zasu iya ɓatawa da duk wani wanda ya ɓata masa, dakuwa zasu tsani Zaleeha da tafi kowa murna. Saboda tsananin ƙyashi da hassadan dayaci Balkeesu kasa cigaba da zama agidan tayi, lokaci guda tayiwa Zaleehan Sallama inda takoma gida, zuciyarta cike da saƙe-saƙe kala-kala. Tun wannan fitowan da Zaleeha tayi na zuwa buɗan kai, daganan bata sake fitowa ko falo ba, abincin da aka kawo mata ma har ɗaki, Raliya takawo mata ta ajiye, sam kasa cin abincin tayi, Zaheera ce taci inda tacika cikinta, itakam babu abun daya shallaketa, tanajin daɗin zaman gidan, babu wani takura, dagaci sai kallo, dama ita tanan tafi kauri, aiki ko na misƙala zarratinne basonshi take ba, wannan dalilin ma yana ɗaya daga cikin abun dayasa ta ƙi komawa gida, domin tasan da zaran takoma tofa aiki za'aita sakata kamar jaka, itakuwa sam bason hakan take ba, ga shi Ziyada ba zama take ba, always tana gidan Hajja ga Zaleeha dake yawan yin wasu aiyukan kuma an aurarta. Saifuddeen kuwa gaba ɗaya wunin yau dasu Ishaq yayisa, don sosai suka zauna don ɗebe masa kewa, kasancewar acikinsu babu wanda baisan matsayin auren Saifuddeen da Zaleehan ba, kowa yasan baso takeyi ba, dan haka nan suka wuni sai dare suka tattafi. Koda Yadawo sallan Isha, kai tsaye falonsa ya wuce, koda yazo falonta ko ƙofar ɗakinta bai kalla ba, dan shima yau ƴan jan ajinnasa suna kusa, duk dacewa yana da buƙatar jinta ajikinsa, amma dole haka zai daure, dan yasan koda yaje ma tofa faɗa zasuyi, shikuwa bayanzu yakeson yafara gwada mata ƴar ƙarfi ba. Koda yashiga haɗaɗɗen bedroom ɗinsa wanka yayi, inda ya kimtsa kansa cikin kayan baccinsa, kwanciya yayi tare da jawo laptop ɗinsa, nan yayi ƴan danne danne, a hankali ya zubawa system ɗin ido, yana kallon motar nan da yasa Hayatuddeen ya liƙa mata na'ura tana tafe har gidan da ta shiga, yaga matasan baki ɗaya sai kuma duk sukayi cikin gidan hakanne ya hanashi damar ganin abinda ke faruwa a cikin gidan. bincike yaci gaba da yi akan gidan da matasan har saida ya samu iya abinda zai samu to amman har yanzu babu ƙwaƙran laifin da za'a kamasu dumu-dumu a ciki haka dai ya haɗa abinda ya samu, kafun daga bisani bacci ɓarawo ya ɗaukesa. A cikin gidan Dalla kuwa,koda yaranshi suka gama yi mishi bayanin abinda ya faru, cikin tsananin tashin hankali yace. "To meyasa!? Waya ɓata min tsarina!? ya akayi haka ta faru?." sai ya kuma shaƙo wuyan Lado dake gabanshi cikin rashin imani yace. "Shekara ɗaya cur ban fatattaka ƴar kowaba, nace muku babu ƴar da zan taɓa a kanta nakeso na gwada lafiyata, meyasa zakuyi min kuskuren da har wani ya gane ya bata tsaro, nafa ce muku a buƙace nake." ingiza Lado yayo ganin yana kakarin mutuwa, shi kuwa Lado tari ya rinƙayi ba sassauci. yayinda gaba ɗaya sauran yaran suka sha jinin jikinsu, shiko Dalla safa da marwa ya farayi a kansu yana wani irin numfashin masifa da tijara da ƙwarewa a dabanci cikin yaƙini da kansho murya a hargitse yace. "Wallahi wallahi sai na girgiza zuƙatan gombawa sai kowa yaji kwatankwacin baƙin cikin da naji, na rantse da ubangijin dake busan numfashi sai na keta haddin ƴan mata huɗu a wuni ɗaya shine fansar budurcin shegiyar yarinyar nan da a kanta wannan sojan yamin dandatsan ɗan akuya." wata iriyar wawuyar tsawa ya tamfatsa musu tare da cewa. "Dole ku nemo min zuƙa-zuƙan ƴan mata huɗu dan na gwada lafiyata a kansu." cikin biyayya da tsoro sukace, "An gama." shi kuwa Dalla a harzuƙe yace. "Ku nemo min su daga yau zuwa mako biyu rak, ita kuwa shegiyar yarinyar nan dan nasan ba namijin da za'a kaiwa ita ya kwana da ita ɗaki ɗaya bai ratsa budurcinta ba, dan haka na ɗage neman har sai nanda wani lokacin zan nemeta in mata fyaɗe mafi muni irin fyaɗen da ban taɓa yiwa ƴar kowaba, zan kwana akanta, kuma kuma kowa sai yayi awa biyu a kanta wannan ganimar samotane." cikin jin daɗin ganimar daya alƙawaranta musu, suka sallameshi suka tafi. A can ɗakin Zaleeha kuwa, duk yanda taso bacci ya ɗauketa abun yaci tura, tayi juyin harta gaji amma bacci yaƙi ɗaukarta, gaba ɗaya zuciyarta cike take da tunani kala-kala,  sosai soyayyarsa ke ƙara yawaita acikin zuciyarta, duk wannan rububin da akeyi da sonsa take kwana take tashi, har zuwa yau batacire rai da samunsa ba, tasa aranta cewa komin daɗewa watarana zata gansa. Tashi zaune tayi ji take kamar korata akeyi daga cikin ɗakin sam bata samu tayi isshen bacci, gyara zamanta tayi tare dakai dubanta ga Zaheera wacce ke kwance akan kujera tanata sharar baccinta, inda tayi ɗai-ɗai da ƙafafunta, ahankali ta dawo da dubanta ga jikinta, sanye take da wata fitinanniyar sleeping gown, irin mai fitar da surar jiki ɗinnan, sosai rigan dake da kalan coffee ta amshi farar fatarta, daga wuyan rigar har zuwa kan ƙirjinta gaba ɗaya net ne irin mai  showing skin ɗinnan,  yayinda kwata-kwata tsayin rigar yakasance iya cinyarta ne, hannu tasa taɗan shafi dogon gashinta dake baje bisa kafaɗunta,   ahankali ta zuro da ƙafafunta ƙasa, tashi daga kan gadon tayi tare da miƙewa tsaye. gaba ɗaya jin ɗakin take ya mata ƙunci, ahankali take tafiya harta ƙarasa jikin ƙofar fita daga ɗakin, ahankali ta murɗa handle ɗin ƙofar tare da sanya key ta buɗe ƙofar,  cikin nutsuwa tafito zuwa falo, ahankali take ɗan takawa harzuwa tsakiyan falon nan taɗan shiga ƙarewa falon kallo, sai alokacinne ma take yaba tsantsar kyawun kayan da Yaya Ahmad ɗin ya saya ma, taga masifar tsaruwar ginin falon, amma saboda yakasance mallaki ga Saifuddeen yasa, ko kaɗan bataji zata yaba tsarin falon da gidan ba, ƙarasawa jikin window'n falon tayi ta tsaya, ahankali taɗan buɗe glass ɗin window'n, take wani irin ni'inmtaccen ƙamshi haɗi da sanyin shuke shuken dake wajen suka daki fuskarta, lumshe idanunta tayi tare da sake manna jikinta da bango tana shaƙan ƙamshin... Saifuddeen kuwa wani iri fitinannan ƙishine ya tasoshi gaba cikin baccinsa. Ahankali Yake buɗe kyawawan idanunsa, hakanan yaji wani irin sanyi na ratsa zuciyarsa, sake buɗe idanunsa yayi tare da sauƙesu akan agogon bangon dake saƙale cikin ɗakin. 1:40 am agogon ya nuna, hakanne yasashi ɗan tashi ya zauna, mamakin farkawarsa adai-dai wannan lokacin yake, jin masifan ƙishirwa na damunsa yajawo kekensa inda ya hau, ya zauna ɗas a kai ya tura kansa har zuwa gaban ɗan madaidaicin fridge din dake cikin ɗakin, koda ya buɗe fridge ɗin gani yayi babu ruwa, gaba ɗaya drinks ne suka cika fridge'n, dolensa haka ya murɗa handle ɗin kofar ɗakin inda yanufi falonsa. Gaban fridgen dake cikin falon ya ƙarasa, inda ya buɗe ya ɗauki goran ruwa, ahankali ya ɓalle murfin tare dakai goran bakinsa,  sosai yasha ruwan saida yaji ya ƙoshi kafun ya aje goran,  aƙoƙarinsa na komawa ɗakinsa ne idanunsa suka gane masa haske acikin falon Zaleeha,  kansa kawai ya girgiza, har zai koma ɗaki kuma, saiya tuna da cewa baya son abar ƙwan wuta akunne matuƙar za'a kwanta yana da kyau adinga kashe ƙoyayen wuta. Ahankali yaƙarasa jikin ƙofar falon nasa ya buɗe,  kekensa ya danna inda yaƙaraso zuwa falon nata, idanunsa ne sukayi masa tozali da bayanta, inda har yanzu take tsaye jikin window. Kallonta yasomayi tundaga ƙasa, santala santalan fararen cinyoyinta ne  suka cika masa idanu, ahankali yasauƙe idanunsa akan shape ɗin bayanta,  inda kyawawan hips ɗinta suka bayyana sosai,  still idanunsa ne suka sauƙa akan dogon gashinta dake baje bisa bayanta. Idanunsa ya lumshe tare da shaƙan daddaɗan ƙamshinta dake shawagi acikin falon, sake buɗe idanunsa yayi inda ya ƙurawa shape ɗin bayanta ido, take yaji gaba ɗaya tsikar jikinsa sun mimmiƙe, lokaci guda wani irin fitinanniyar sha'awa ya taso masa. Take yaji wani abu na harbawa acikin jikinsa. Zaleeha kuwa ɗan gajiya da tsayuwan tayi hakan yasa ta juyo dan dawowa cikin falon, kanta aƙasa dan kwata-kwata bata tsammaci ganin wani awannan lokacin ba. Kusan numfashin Saifuddeen ne yaso ƙwacewa alokacin da idanunsa sukayi masa tozali da cikakkun breast ɗinta, wanda suka bayyana kansu ta cikin rigar hartakai ga ana iya ganin kusan rabinsu ta saman rigar, uwa uba ga shatin nipples ɗinta daya bayyana raɗau tacikin lafaffiyar rigar dake jikinta. Wani irin yaarr yaaarr haka yaji ajikinsa, take wani abu ya mamaye gaba ɗaya ilahirin jikinsa, batare daya saniba wani irin numfashi ya ƙwace masa. Jin fusgar numfashin mutum yasa Zaleeha ɗago kanta atsorace, ƙara tasake, sakamakon ganinsa da tayi, tare da saurin ja da baya, sam bata tsammaci ganinsa awannan lokacin ba. Da sauri ta sanya hannu ta dafe ƙirjita, cikin tsoro haɗi da bugun zuciyarta daya tsananta bugawa,  ajiyar zuciya take sauƙewa, sosai ganinsa ya tsoratata, shikuwa Saifuddeen tsuke fuska yayi tare da kafeta da mayan idanunsa, wanda lokaci guda suka sanja launi, inda suka tashi daga fafare zuwa wasu kalan na daban. a fakaice yake kallon ƙirjinta, wanda yake ɗagowa ahankali- hankali yasa, tabbas tsoratan da tayine yasa hakan,  laɓɓansa ya cija tare da yamutsa fuska kana ya sanya hannu ya ɗan shafa kekyawan sajenshi da ya kwanta lib-lib, cikin wani irin yanayi yasake kallonta, saidai wannan karon bai yarda yasauƙe idanunsa akan beautiful breast ɗinta dasuke mugun rikirkitashi ba, musamman ma shatin nipples ɗinta, wanda idan ya kalla sai jijiyar jikinsa ta harba. Shiyasa ya kauda kanshi dan bafa yason raini, kada tayi zaton sha'awarta ke rinjayarsa kada kuma ta ɗaukeshi mayen mace. Ɗan janye hannunta daga kanta tayi tare da dubansa, lokaci guda ta haɗe fuska tare da sanya hannu ta kama waist ɗinta. Cikin faɗa da tsiwa wanda dama tuntuni suke kwance aƙasan zuciyarta ga kuma tsoro baki ta murguɗa mishi tare da cewa. "Ae bai kamata bama nayi mamakin ganinka at this time ba, because aljani koda yaushe yana nan kuma zaije ko ina kuma zaiyi abinda yake so!." Hararansa tayi tare daɗan juya idanunta cikin halin ko inkula tace. "Meye kake wani kallona? idan ma kai mayene wallahi saidai kaci kanka domin nidai nafi ƙarfinka, kurwata kurrrr  ni wallahi ka dena tsareni da waɗannan mayatattun ida nun naka." Taƙare maganar tana jujjuya masa idanu, haɗi da kama ƙugunta, sam tagama mantawa da shigar dake jikinta kwata kwata. Shikuwa Saifuddeen murmushin ƙasan zuciya yayi kana ya lumshe idanunsa tare da buɗewa yakuma watsa mata su, da sauri ta ɗauke idanunta daga kallonsa tare dajin wata irin faɗuwar gaba ya rusketa kwarjininshi da haibarsa suka mamaye fuskarsa a take taji shakkarshi da shayinshi. Lokaci guda taji wani irin abu yana bi ta cikin jikinta har zuwa cikin zuciyarta dake harbawa da sauri-sauri. Ahankali ya danna madannin kekensa inda yasoma nufowa gareta, ganin haka yasa tasoma ja da baya baya, still shikuma baidaina biyota ba, babu abun dayaso gusar da tunaninta kamar yanda ƙwayan idanunsa suka sanja launi daga farare zuwa ja, sannan gaba ɗaya sun rikiɗe sun canja launi zuwa yanayin bacci. Saura baifi taku uku tsakaninsu ba, ta juya inda ta buɗe ƙofar ɗakinta ta faɗa ciki da gudu, tana shiga da sauri ta murzawa ƙofar ɗakin key. Ganin alaman saka key aƙofar yasanyashi lumshe idanunsa tare yin murmushin mugunta da sanya hannunsa ya dafe goshinsa, ahankali yajuya yanufi ɓangarensa, idanunsa tuni sun rufe wani irin masifaffen sha'awa ne ke taso masa irin wanda bai taɓa ji ba kuwa. A ranshi yake cewa. "Farar kura ba ga tsoro ga son bada tsoro, wai ita in an barta ni zata razana, fitinanniya mai bakin tsiwa, yarinya zanyi mgninki bakin zai mace." Adaddafe yasamu yahau kan gadonsa, lumshe idanunsa yayi tare dayin kwanciyar rubda ciki, sosai yakejin wani matsanancin feeling, yayinda dazaran ya kulle idanunsa, hoton haɗaɗɗen surar ƙirjinta dana bayanta keyi masa gizo, tabbas  shikam ya yaba da kyawu haɗi da cikar surar Zaleeha, ƙam haka ya ruggume pillow, sosai yakejin matsananfin feelings ɗinta, tunowa da yanda ya tsotsi laɓɓanta jiya, shiya sanya ya ƙara rikicewa, sosai yake sonjin ɗuminta acikin jikinsa, saidai kuma bashi da wani zaɓi wanda ya wuce haƙuri, dan shi tunani ma yake duk randa ya kusan ceta yaga ta kanshi dan yaga alamun tara mishi jama'a zatayi. Ɓangaren Zaleeha kuwa tana murzawa ƙofar key, da gudu ta haura kan gado tare da shigewa cikin blanket, ƙam haka ta kulle idanunta gaba ɗaya jikinta karkarwa yakeyi, sai alokacinne ma tatuna da irin shigar dake jikinta, take wani irin abu ya tokare maƙoshinta, tashi zaune tayi tare da duban kanta, ganin rabin ƙirjinta awaje, yasa ta cije baki, cikin takaici haɗi da kishin kanta tace. "Sam baicancanci yaga surata ba, wayyo ni maiyasama nafita ne?." Tsuka tayi tare da komawa ta kwanta, baccin tsorone ya ɗauketa batare da ta shiryawa hakan ba. Shikuwa Saifuddeen saida yasha artabu da jikinshi da zuciyarshi sosai kafun ya iya maida bacci. Washe gari. Kamar yanda takeyi tun da tazo gidan haka yauma tayi, tana gama idar da sallah tatafi ɓangaren Ummi inda tagaisheta. Yau ɗinma Ummi cikin so da ƙauna ta amsa mata gaisuwarta, a falo ta haɗu da Saifudddeen da Hayatuddeen bisa dukkan alamu daga masallaci suke, cikin sakin fuska Hayatuddeen yace, "Barka da safiya Aunty Zaleeha." ɗan tsayawa tayi fuska a sake tace. "Barka dai autan Ummi." murmushi yayi tare da cewa. "Ya amarci da gajiyan biki." hararansho taƴi cikin sanyi ta ratsa gefen Hamma Saifuddeen ɗin harara ta cillamishi, sai kuma tayi wuf ta wuceshi kamar dai tsoro take kar ya cabketa abinma dariya ya basu kana suka bita da ido. daga ɓangaren na Ummi kaitsaye part dinsu ta  dawo, komawa tayi tanaɗe akan gado inda tacigaba da baccinta. Acan gidan su Zaleeha kuwa sai jiya Mama tadawo daga tafiyanta da tayi, Baba Malam dai ko sannu baice da ita ba, koda ya lura cewa Zaheera bata gidan, tana can gidan Zaleeha, sosai ransa ya ɓaci, nanfa yasa Ya Ameenu Habu akan su kwashi kayayyakinta na aure da motocinta su kai maita kana su ɗauko Zahira sannan su ƙara yiwa Zaleehan nasiha inda yaje. Hakan kuwa akayi, tuni Ya Ameenu da Habu sukatafi dan ɗauko Zaheeran bayan duk sun lodo kayan aurenta a motocintan. Koda sukaje gidan nasu Saifuddeen sai Ya Aminun ya bawa Habu kuɗi yacewa Habu ya hau keke napep ya koma ya ɗauko motarshi su samu wacce zasu koma da ita tunda duk motoci biyun da suka zo dasu na Zaleehan ne ɗaya na cikin kayan aurenta ɗaya kuma wacce Ya Ahmad ɗinta ya saya mata, Ya Aminu na fitowa cikin motar ya nufi wurin maigaɗinsu akan yaje ya mishi sallama da masu gidan a nan suka haɗu da Ahmad, inda suka gaisa cikin girmamawa da mutum ta juna, Ahmad ne yayi masa jagora har cikin gidan, saida Ya Ameena yafara zuwa ɓangaren Ummi tukunna, cikin mutum tawa ya gaida ta, sannan yayi mata bayanin cewa yazo ɗaukar Zaheera ne,  sosai Ummi taji daɗin karramata da yayi, nan tasake aminta da tarbiyan gidan Baba Malam ɗin, Ahmad ne yayiwa Ya Ameenu jagora zuwa ɓangaren Zaleehan, don kuwa Saifuddeen bayanan, sun tafi meeting ɗin ƙungiyarsu na Jonapwd shida Ishaq. Sosai Zaleeha taji daɗin ganin yayan nata, saidai kuma jin cewa Zaheera yazo ɗauka, yasanya taɗan ɓata fuska, saidai kuma bata isa cewa komai ba, sanin cewa Ya Ameenun nada zafi sosai, babu ruwansa yanzu saiya solleta soso da sabulu. Haka Zaheera ma ranta baiso ba, don dai kawai Ya Ameenun ne yazo da kansa, amma da wanine bazata bisa ba, don ita ke gadin Zaleeha a cewarsu a yadda suka tsara kenan wai ai duk nacinsa bazai zo inda takeba in Zahira nan kuma da ita aketa plant ɗin yadda Zaleeha zata gudu, Haka dole ta haɗo kayanta, Gyara zama ya Ameenu yayi, cikin kulawa haɗi da kwantar da murya, yashigayiwa Zaleehan nasiha, dayi mata nuni akan tabi mijinta, idan ya umarceta da yinnabu matuƙar bai saɓawa shariya ba yace tayi to koda bataso tayi, domin hakan shine dai-dai domin al'jannarta na ƙarƙashin diga-diginsa . Itadai Zaleeha jinsa kawai take, amma bata ɗauƙa, koda yazo tafiya har compound ɗin gidan ta rakosu, nan kuma yasa Hayatuddeen da Imran dasu Zakariyya kwashe kayayyakinta kab suka shigar mata, sannan ya bata car keys ɗinta duka biyu a hannunta, godiya tayi tare da cewa ya gaishe mata da Ƴar uwarta Maryam. Haka Ya Ameenu yatasa Zaheera suka bar cikin gidan, shikansa ya yaba da tsarin gidan, musamman ma part ɗin Zaleeha wanda yayi matuƙar kyau, shida kansa ya ƙyasa, ya kuma yabawa Saifuddeen sosai, don bakowani namiji bane zai iya ɓarnatar da dukiyarsa wajen ƙawata gida mai kyau kamar haka ba. Tafiyan Zaheera yasa Zaleeha duk taji gidan bayayi mata daɗi, hakanan taji komai ya tsaya mata, batasan dacewa motsin Zaheeran na ɗebe mata kewa ba, sai ayanzu da Zaheeran tatafi, haka ta koma ɗaki ta kwanta, zuciyarta cike da saƙe-saƙe kala-kala. Tananan ƙule aɗaki har akayi sallan isha, Nanfa wani irin tsoro yashiga diro mata, take fargaba ta cika zuciyarta, sam batajin zata iya kwana itakaɗai aɗakin batare da wani nata ba, sosai tsoron sa yashiga zuciyarta, tabbas ayanda taga cikin idanunsa jiya to idan tayi wasa komai zai iya aikata mata, abanza saiya rabata da virginty ɗinta, shikenan kuma daganan yagama cutanta, dan tasa aranta cewa bamakawa daga ranan daya yayi disvirgin ɗinta tofa shikenan itakam ta sallama rai da rayuwa, don baƙinciki ne zaiyi ajalinta tabbas. Tashi tayi daga kan sallayan tare da kai dubanta jikin ƙofar ɗakin, ganin babu key ajikin ƙofar yasa gaba ɗaya hankalinta ya ƙara tashi,  atsorace tashiga neman key ɗin amma bata gani ba. Ƙirjintane yatsananta bugu alokacin da taji motsin mutum a falonta. Shikuwa Saifuddeen lokacin dawowansa kenan daga masallaci, kaitsaye ɗakinsa ya wuce, dan yanaso yaɗan watsa ruwa, kafun ya ya ɗa ci abinci. Jin motsin buɗe kofar falonsa, dakuma rufewa yasanya taɗanji zuciyarta tayi sanyi, cikin hanzari ta ɗauki blanket da pillow, saikuma phone ɗinta, saɗab-saɗab tafito daga cikin ɗakin, ahanzarce tayi hanyar fita daga cikin falon, tana samun kanta aɗan compound ɗin shashin nata kuwa ta saki ajiyar zuciya,  kaitsaye garden ɗin dake cikin part ɗin nata ta nufa wanda yake cike da sanyi da sauraye, kan wata kujera dake ɗan cikin garden din ta kwanta, tare da jawo blanket ta rufa jikinta, ɗaura kanta tayi akan pillow tare da sauƙe ajiyar zuciya, ta dai gwammace kwana awajen da dai ta tsaya aciki ya illata mata rayuwa, zata jure komai amma bazata iya jure abinda zai iya mata ba, hakanan bata tsaya wani mugu yayi disvirgin ɗinta ba tunda ta duba ɗaya ɗakinma babu key sai tayi zaton shine ya zaresu dan karta rufe ƙofa ya samu damar shigowa ya mata fyaɗe injita da faɗi. Raliya kuwa wacce tazo rufe window'n ɗakinta dake abu ɗe ne taga kaman wulgawan mutum ya shiga cikin garden, kanta tasake zurowa ta cikin window'n, nan idanunta suka gane mata Zaleeha dake ƙoƙarin kwanciya akan wata kujeran ƙarfe. Mamakine yakusan  kasheta awajen, sosai abun ya ɗaure mata kai, komawa cikin ɗakin nata tayi ta zauna tare dayin jigum, me hakan yake nufi kenan? tsanar da Zaleeha tayiwa ɗan uwanta har yakai wanda zataƙi haɗa shumfuɗa dashi? har ta gwammaci kwana acikin sauro da ciyawi da sanyi a kan kujerar ƙarfe akan ta kwana dashi. Kanta ta jinjina tare da rumtse idanunta wanda suka ciko da ƙwalla, sam bahaka ta ke wa ɗan uwannata fata ba, babban burinta shine yasamu ingantaccen kulawa daga wajen matar tasa amma meyasa Zaleeha ke gudunsa? kwaffa tayi tare da cewa. "Ko ya zakiyi wlh in sha Allah sai dai ya raɓi jikinki in Allah ya yarda duk iskancinki kin shiga hannu kenan mutu ka raba, ato sai yaci sadakinshi." Tana faɗin haka sai kuma ta miƙe da sauri ta nufi.....! Littafina na kune in kin ganshi a wojema na satane, turo ɗari 300 ta wannan no 09097853276 ko ka/kiyi min transfer'n 300 ta asusuna na 0005388578 jaiz bank Aisha Aliyu Garkuwa. Wanda ya karanta na sata Yaseeeen doguwa. By *GARKUWAR FULANI* [9/9, 9:05 PM] +234 806 222 4030: Murmushi Baba Malam yayi irin nasu na manya, kana ya ɗanyi jim, haƙiƙa fasa auren Zaleeha bazai rage komai ba face mutuncinsa da kimarshi, mutuƙar kuwa aka fasa auren to tabbas ita da mahaifiyarta sun samu abun da suke so, sam shikuma bazai lamunci hakan ba, gyara zamansa yayi tare da kai dubansa ga su Baffa Ali da Malam Ashiru. Cikin nutsuwa haɗi da kamala yace. "Haƙiƙa nafahimci me kukeji agame da wannan auren, saidai kada ku manta mu daku ɗin kamar ƴan uwa muke,  dukanmu tsofaffine masu dattako da sanin ya kamata,  amatsayina kuma na mahaifi ga Zaleeha zan ƙirata na zaunar da ita nayi mata nasiha, insha Allah nasan zata fahimta, dan Allah kuyi haƙuri, rashin tunanine kawai irin na yaran zamani!." Ajiyar zuciya su Baffa Ali suka sauƙe, cikin sanyin murya haɗi da fahimtar Baba Malam ɗin, Baffa Ali yace, "shikenan Malam Basheer babu komai, Allah yasa auren ya zama al'khairi agaresu, Allah kuma ya sawa Zaleeha so da ƙaunar Saifuddeen acikin zuciyarta, don shikam yana sonta sosai, fatan mu shine auren nasu yayi al'barka!." Da "Ameen Ameen!." suka amsa su dukansu,  inda Baba Malam ya sauƙe ajiyar zuciya, sosai yaji girman na iyayen Saifuddeen ya ƙaru acikin idanunsa, nan suka ɗan tattauna maganganu masu muhimmanci, daga nan kuwa su Baffa Ali sukayiwa Baba Malam ɗin sallama,  har bakin motarsu Baba Malam ya rakosu, inda bai dawo cikin gida ba saida yaga tafiyarsu. Zama yayi akan ɗaya daga cikin tausassun royal chairs ɗin da suka ƙawata haɗaɗɗen falon nasa, bayansa ya jingina da jikin kujeran tare da lumshe idanunsa,  cikin ransa haka yakejin ba daɗi, tunda yake baitaɓa sanya ranan auren ɗansa ko ƴarsa daga baya kuma akazo da maganar fasawa ba sai akan Zaleeha! duk kuma a dalilin taurin kai irin nata, tabbas Zaleeha tanason sashi yaji kunya a idanun mutanen da suke matuƙar ganin ƙimansa, amma babu komai zaiyi abun tubkar hanci tunda wuri,  wayarsa dake cikin al'jihun rigarsa ya laluɓo inda ya dannawa nombern Mama ƙira, bugu uku ana huɗu Mama ta ɗauki ƙiran, batare daya jira komai daga gareta ba yace. "Kituromin Zaleeha." kitt ya kashe wayan, don sam baison abun dazai ɓata ransa da daren nan. Bayan kamar minti shida dai-dai Mama tashigo cikin falon hannunta ɗauke da ɗan madaidaicin tray wanda samansa ke ɗauke da flask da kuma ƙananan cup guda biyu,  bakinta ɗauke da sallama ta ƙaraso cikin falon, inda ta jawo wani babban table dake tsakiyan falon ta kawosa har gaban Baba Malam ɗin, nan ta ɗaura ɗan ƙaramin tray din akan table ɗin,  duban Baba Malam tayi fuska ɗauke da Murmushi tace. "Barka da hutawa!." Shima Baba Malam ɗin fuskarsa ɗauke da murmushi, ya jinjina mata kai alaman ya amsa. Su Baffa Ali kuwa koda suka isa gidan nasu Saifudden kai tsaye ɓangaren Ummi suka nufa,  zaune suka isketa ababban falon nata, gefenta kuwa Hayatudeen ne wanda keta faman buga game ɗin Drok Stack Ball awayarsa. ganinsu yasa Hayatuddeen ya gaishesu cikin ladabi, don kuwa hadda Dirankadi akazo,  nan ya miƙe ya haura sama zuwa ɗakinsa. Ummi kuwa tashi tayi ta kawo musu drinks masu ɗan sanyi,   nan ta zauna suka shiga ɗan gaisawa, musamman da Dirankaɗi wanda suka jima basu haɗu ba. Bayan sungama gaisawa ne, Dirankaɗi ya gyara zamansa tare da fuskantar Ummi'n, sanin cewa ita ɗin mai yawan haƙuri da sauƙin kai ne yasanyasa tausasa lafuzansa, tayanda zata fahimcesa sosai, ahankali yace. "Kamar yanda kika buƙata da muje gidan su Zaleeha, munje munkuma sanar musu cewar mun janye batun auren!.". Ajiyan zuciya sauƙe a hankali tare da cewa. "Alhamdulillah". murmushi suka ɗanyi, sai kuma Dirankadi ya ɗan numfasa tare da cewa. "Kiyi haƙuri Hajiya..  kisa aranki cewa auren Saifuddeen da Zaleeha haɗine na Allah bawai yin kanmu ba, sannan kada ki manta ance matar mutum kabarinsa, sannan idan Allah Ya nufa cewa Saifuddeen sai ya auri Zaleeha bamu isa hanawa ba." shiru tayi jiki a mace taci gaba da sauraronshi. "Tabbas nasan mekikeji nakuma fahimci irin fargaban da kike ciki, ƙwarai kowacce uwa bazata taɓa son wani abu dazai cutar mata da ɗanta ba, nasan kina gujewa Saifuddeen auren Zaleeha ne badon komai ba saidan, kina jin tsoron abunda kaje kazo, da kuma irin tsananin ƙiyayyar da Zaleehan ke nuna masa,  ƙwarai hakan abun tsorone to amma kada ki manta, babu wani abu dazai samu bawa me kyau ko akasinsa,  face dama tuntuni anrubuta acikin littafin ƙaddaransa." Kai ta gyaɗa tare da cewa . "Haƙƙun". Cikin jin daɗin tana gamsuwa yaci ga da cewa. "Wani baya taɓa iya cutar da wani harsai Allah Ne ya tsara hakan,  saboda haka inaso ki kwantar da hankalinki, munyi magana ta fahimta da mahaifin yarinyar, mutum ne shi mai tsananin dattako da kamala, kema kinsan hakan tuntuni, ya ƙasƙantar da kansa ya bamu haƙuri, ya haɗamu da Allah cewa kada a fasa auren! yakuma taushemu da lafuzza masu daɗi, saboda haka mu dai mun aminta cewa Saifuddeen zai auri Zaleeha, saboda haka yana ɗaya daga cikin ƙaddaransa, komai zai wuce kuma watarana sai labari, kema inaso kisa aranki cewa Insha Allah auren Saifuddeen da Zaleeha al'khairine mai tarin yawa, wanda zaisa dukkanmu farinciki anan gaba,   mudai addu'an al'khairi yadace munayi musu ako da yaushe!." Baffa Aline yaɗan nisa tare da amsawa da cewa. "Ƙwarai kuwa, abun da Dirankaɗi ya faɗa gaskiyace, haƙiƙa dukanmu nan munsan cewa ke uwa ta gari ce,  munsanki da haƙuri Ummi, dan Allah inaso ki ƙara akan nada, ki-kumayi duba da irin tarin soyayyar da Saifuddeen keyiwa yarinyarnan tunfa suna ƙanana, kuma rauninki zaisa Saifuddeen fasa auren nan!." Malam Ashiru ne yace. "Ƙwarai kuwa, ayanzu dai fatan al'khairi da sa al'barka kawai suke buƙata daga garemu." Ajiyar zuciya Ummi ta sauƙe tare dayin ƙasa da kanta, sosai taji zuciyarta tayi mata nauyi, yayinda matsanancin rauni ya bayyana acikin idanunta, haƙiƙa ita abu ɗaya take gujewa Saifuddeen shine halin dazai faɗa bayan aurensa da Zaleeha, matuƙar bata sanja hali ba, tasan Saifuddeen bazaiji daɗin zaman auren ba, wanda ita kuma duk wani fata da burinta baiwuce Saifuddeen ɗinta ya samu mace tagari, mai share hawayensa. Hawayen dake ƙoƙarin cika idanunta ta shanye tare da ɗan sakin murmushi, cikin sanyi tace. "Babu komai, duk yanda kukace shikenan, dama ni baƙin Zaleeha nake ba kawai dai munanan kalamai da ƙudurinta akan Saifuddeen shine ke bani tsoro, amma zantayi musu addu'a Allah yasa auren yazama alkhairi, wanda kowa zai amfana dashi!." Cikin jin daɗin sauƙin kai irin na Ummin dukansu suka amsa da "Ameen Ameen." Nan Dirankadi yace acigaba da shirye shiryen biki kada afasa komai da akayi niya, baiwani jima agidan ba yashiga motarsa inda ya nufi gida, su kuwa su Baffa Ali can cikin BQ suka sauƙa, saboda dare yayi babu yiyuwar komawarsu Dukku aranan, saidai gobe da safe zasu kama hanya. Jin ƙiran da Baban nata keyi mata yasanya taji gabanta ya faɗi, take tsoro ya shigeta saidai kuma babu yanda ta iya dolenta ta amsa ƙiran nasa, zumbuleliyar hijab ɗinta ta zura, kana tanufi ɓangaren mahaifin nasu. Da sallama ɗauke abakinta ta kutsa kanta cikin falon,   cikin sanyi Baba Malam ya amsa mata,   ƙarasowa tayi inda ta zauna akan lallausan carpet ɗin dake malale bisa tsakiyan falon, duƙunƙune jikinta tayi acikin hijabin, cikin ƴar siririyar muryarta dake rawa tace. "Barka da dare Baba Malam!." Kansa kawai ya jinjina mata alamar "Yauwa." Aƙalla ta ɗau sama da mintuna 5 baice da ita komai ba, nanfa bugawar zuciyarta ya tsananta, don amatuƙar tsorace take. Gyara zama Baba Malam yayi tare da fuskantar ta,  cikin kulawa yaƙira sunanta. Ɗagowa tayi ta kalleshi tare da amsa masa murya na rawa jiki asanyaye. Ajiyar zuciya Baba Malam ya sauƙe tare da yi mata duban tsab, cikin son tausasa lafuzansa agareta dan yi mta nasihar da wala Allah imaninta zai sabunta cikin kula yace. "Haƙiƙa kowani uba yana al'fahari da ƴarsa ko ɗansa matuƙar sukayi masa biyayya,." Sosai lafazinshi ya ratsa jikinta, Shi kuwa cigaba yayi da cewa.   "Bazance bana al'fahari dake ba Zaleeha saboda ke jininace, sannan kuma ko ba komai kin amshi zaɓin dana baki, kin kuma yi na am, saidai kuma labari yazo kunnena akan cewar kina rubuta saƙo irin na ɓaƙaƙen maganganu da kuma gargaɗi da barazana da kisan kai kina turawa Saifuddeen". Tuni jikinta yake tsuma.   "Kada ki watsamin ƙasa a ido Zaleeha! Dan in kikamin haka ,wallahi Allah zan barranta dake, kada kimin fuska biyu. tabbas nasan cewa rashin sanin wanene Saifuddeen agareki shiyasa kike wulaƙantasa, yanunamiki ƙauna da gata tun kina ƴar ƙanƙanuwan yarinya, haka kuma har kawo yanzu bai janye ƙaunarsa daga gareki ba,  Saifuddeen maganarci ne wanda nayi imani samun kamarsa nada matuƙar wahala, ba'akowani gida ne ake haihuwar irin Saifuddeen ba haka kuma irinsu basu da yawa acikin al'umma, nazaɓa miki Saifuddeen amatsayin mijine saboda nasan bazaki taɓa danasanin aurensa ba, Saifuddeen bazai barki kiyi baƙinciki ba Zaleeha." Tuni hawaye ke kwaranyo mata a ranta take faɗin. "Wannan musakin wanne farin ciki zai samar min,mutun da bashi da bakin da zai furta min kalaman so, mutumin dake kamar dutse duk daɗin kalmar da zan masa ba ji zaiba, haka zan rayu dashi babu so bare soyayya da ƙauna! muryar baban natane ya katse mata hasashenta. "Zaleeha kina ganin nakasasshe ne ko, to Saifuddeen da kike gani shi zai zame miki GARKUWA sannan bongo majingina na rayuwarki,  shin Zaleeha menene aibun Saifuddeen dan yakasance Nakasashshe? saboda shi nakasashshene shiyasa kawai kike gudunsa? Baki san cewa Nakasa Ba Kasawa Bace Zaleeha, kuma babu nakasasshe sai kasasshe musamman nakasa irin ta Saifuddeen da bata shafi lafiyarsa ba, sannan nakasar zuci itace nakasa ba wai ta gangar jiki ba,  Saifuddeen yana da kyakkyawar zuciya, kyawawan ɗabi'u, kyawawan halayya, ga  wadatan zuci  duk ya haɗa in kuma kyau ne tako ina Allah ya mishi kyau da haiba, haƙiƙa amatsayina na uba mahaifinki, ina matuƙar yi miki kwaɗayin samun managarcin miji kamar Saifuddeen, sanin cewa miƙa aurenki ga Saifuddeen danayi bazaisa nayi dana sani ba, shiya zuciyata ta aminta da shi sosai,  dan Allah Zaleeha, ki nutsu ki dawo cikin hankalinki, ki watsar da duk wani buri ki rungumi auren Saifuddeen amatsayin ƙaddarar rayuwarki,  kin kuma san idan kikayi haka Allah bazai bari ki taɓe ba,  ni mahaifinki ne Zaleeha, idan ban nusar dake ba, babu wani wanda zai nusar dake, saboda haka maganan tura ɓaƙaƙen maganganu ga Saifuddeen banasonshi dan Allah ki daina kinji ko Mamana?." A hankali ta gyaɗa kanta alamar to yayinda cikin zuciyarta kamar ta mutu dan baƙin ciki. "Saura ƴan kwanaki kaɗan yazamanto miji agareki saboda haka yazama dole ki girmamasa kamar yanda kike girmamani harma fiye da haka domin shi mijinki ne kuma al'jannarki tana ƙarkashi diga-diginshi ,sai ya ɗaga zaki shiga". A ranta take cewa. "Wannan gurgun kam ai ɗaga ƙafarma ba iyawa zaiba." hannu tasa tana share hawayenta jin Baba malam ɗiɓ yaci gaba da cewa. "Saboda matsayinsa na miji agareki yazama dole kiyi masa biyayya da ɗa'a, koda wasa kada kice zaki bijirewa umarninsa, ƙin bin umarninsa tamkar saɓawa Allah Ne saboda haka ki kiyaye!." Tuni hawaye sun wanke fuskar Zaleeha, sosai zuciyarta keyi mata ƙuna so take tasaki kuka mai sauti, hakan yasa tasanya hannuwanta duka biyu ta toshe bakinta, gudun kada kukan ya fito, kai kawai taketa gyaɗawa kamar Ƙadangaruwa. Ganin haka yasa Baba Malam cewa. "Tashi kije, sannan koda wasa kada ki taɓa mantawa da maganganu na, domin kuwa idan akace yau bana raye babu wani wanda zai faɗamiki makamancinsu." still kai ta gyaɗan Da sauri ta-tashi ta fice daga cikin falon, tana rufo ƙofar falon tashiga tafiya cikin yanayi na gudu-gudu sauri-sauri, koda ta shiga falo, tsaye ta samu Mama tanata kaiwa da komowa,  Mama naganin Zaleehan tayo kanta, cike dason tambayarta me Baba Malam ɗin yace mata, saidai me tuni Zaleeha ta shiga ɗakinta inda ta rufo ƙofar tare da murza mata key, sulalewa tayi ajikin ƙofar tare da sakin kuka mai sauti,   galala haka Mama tasaki baki tana kallon ƙofar ɗakin Zaleehan, kana daga inda take tsaye tanajiyo sautin kukan da  Zaleehan keyi, rantane yayi matuƙar ɓaci, domin tasan babu wani abu dazaisa Zaleeha kuka haka, idan ba maganar auren wancan nakasashshen ba, gashi tanaji tana gani aka kwashi kayan Abdussalam aka meda, tsuka tayi cike da baƙin ciki haɗi da takaici ta wuce ɗakinta. Kuka sosai Zaleeha tayi harsaida muryarta ta dashe, lokaci guda wani irin zazzafan ciwon kai ya kawo mata ziyara, gaba ɗaya ƙwaƙwalwarta ta toshe harta rasa ma tunanin me zatayi, kullum kwanan duniya soyayyarsa ne keyi mata tsaye acikin rai da zuciyarta, sannan gefe guda kuwa ga yanda rayuwa keneman juya mata baya, tahanyar haɗa ta aure da wani wanda takejin tsanarsa acikin zuciyarta fiye da kowa. Da ƙyar ta iya tashi daga jikin ƙofar, haka ta nufi bathroom, ko gani sosai bata iyawa saboda yanda idanunta suka kumbura sukayi luhu-luhu dasu,  wanke fuskarta tayi tare da dawowa ta kwanta luf akan lallausan gadonta,  sosai kanta ke ciwo kamar zai rabe gida biyu haka takeji, gawani irin zazzaɓi daya sauƙar mata, babban blanket ta jawo tare da rufe jikinta, kanta ta tura acikin pillow, sannu ahankali take fitar da sheshsheƙan kuka, cikin haka wani bacci wanda sam batayishi cikin daɗin rai ba yazo ya ɗauketa. ** Yau ya kama saura kwana biyu biki, inda ake ta hidima haɗi da shirye-shirye daga ɓangarori guda biyun,  gidan su Saifuddeen sosai ake hidima inda tuni ƴan uwansu dake nesa sun zo, nanfa shirin biki ya ƙara armishi, ɓangaren Ango Saifuddeen da abokansa kuwa sunshiga busy sosai, babuma kamar yashi Saifuddeen, gaba ɗaya yanzu bashida wani lokaci koda na hutawa ne, yadage tuƙuru wajen ganin yaƙawata bikin nasa, inda yaketa ɓarnatar da kuɗi wajen ganin ya ƙawatar da kansa da kuma amaryarsa,  gudumawa yake samu sosai takota ina, wanda abun har mamaki yake bashi, sam shi baison mutane suna wahalar da kansu akanshi, musamman ma akan auren nasa yafiso yayi komai da kanshi, haka ƙungiyarsu ta Jonapwd ma ta basa gudumawarta mai tarin yawa, wanda bisa dole ya amsa, don ƙa'idar ƙungiyanne dazaran abu ya samu mutum na hidima, walau farin ciki walau akasinsa, to fa saisun bada nasu taimakon suma. Birnin gombe da kewaye duk sun cika sun ɗauka batun auren Zaleeha da Saifuddeen wanda aketa tallashi a dukkan gidajen Radio kama daganan FM Gombe, PROGRESS, RAYPOWER, AMANA uwa uba, vision FM gidan radio su Zaleeha, yan uwa ƙawaye maƙota ,duk anji labari, Bilkeesu kuwa da gangan ta sanarwa duniya mijin da Zaleeha zata aura nakasasshe ne, wannan abun ya ƙara tada hankalin Zaleeha. Rashida kuwa tuni ta gayyato ƙawayensu baki ɗaya harda waɗanda sukayi aure, haiƙan gadaran suketa shiryawa bikin ita da sauran ƙawayen nasu. Kamar yanda ake ta shirye shirye shiryen biki agidan nasu Saifuddeen cike da farin ciki, aɓangaren gidansu Zaleeha kuwa abun ya banbanta, domin kuwa Baba Malam da Mamy haɗi da su Ya Ahmad ne kaɗai suke shirin auren, sai kuma Mamy wanda tazama kamar itace uwar amarya, don Mama kam fir tamaƙi zama agidan hakanan ta tsiro da tafiya garinsu, tayi hakanne kuma don bazata iya juran tarin baƙin cikin dake tunkarota ba, sam Baba Malam baihanata ba, dan yasan hanatan ma wani babban bala'i zai zama, kuma tama tafi ta basu fili ayi komai ba fitina, shiyasan tunda Mamy nanan bai da muwa da tafiyar Mama. Ita kuwa Mama bazama tayi gidan bokayenta. Yau Baba Malam yace aje ayiwa Amarya Zaleeha jere, saboda haka tun safe Aunty Lubna da kuma Maryam, sai wata Aunty Aseeya wacce take ƙanwar Mamy sai Aunty Shatu suka kimtsa don zuwa yin jeren,   cikin motar Aunty Aseeyan suka shiga, inda aka haɗasu da ƙatuwar motar dake cike da kayan na Zaleeha wanda su Baba Malam ne ya ƙara matasu duk dan wai ta kwantar da hankalinta, daga gefe kuwa musamman Ya Ahmad yayiwa wani babban company magana, wanda suke da ma'aikata wanda suka iya tsara ɗaki, nan yaɗauki hayan ma'aikata guda biyu wanda sune zasu tsarawa Zaleehan ɗakin nata. Koda suka isa gidan nasu Saifuddeen wanda sosai ya amshi gyaran da akayi masa, Ummi da kanta ta amashesu, inda tayi Musu tarba me kyau, sosai sukaji daɗin hakan, inda Maryam tacika da farin ciki, domin kuwa sosai taji daɗin karamcin Ummin, dan tasan Zaleeha ta dace da uwar miji, sannan tasan Ummi bazata bar ƴar uwartata ta wulaƙanta ba,   Raihana mutan Kd da Adda Rahma matar Dr Ummi tasanya su kaisu zuwa ɓangaren Zaleeha,   koda sukaje part ɗin da Zaleehan zata zauna sosai suka cika da mamakin yanda aka ƙawata part ɗin, sosai part ɗin yayi kyau, anyi masa tsari mai ɗaukar hankali, inda aka ƙawata komai dake cikinsa,  tabbas sun yaba da haɗuwar part ɗin na Zaleeha, sunkuma yarda cewa Saifuddeen masoyine agareta, don ko ba a faɗa musu ba sunsan sosai ya ɓarnatar da dukiyansa wajen ƙawata wajen,    tuni ma'aikatan da Ya Ahmad ya turo suka haɗu da maikatan da Salisu ya ɗauko sun shiga aikinsu na shirya wajen don kuwa har sun gama kimtsa falo,  sabida su biyarne dan haka aikin ke gudu, sosai falon ya tsaru haɗaɗɗen falone wanda aka ƙawata gaba ɗaya jikin bangon da wani haɗaɗɗen magic paint me tsananin kyau, yayinda aka watsa wasu   haɗaɗɗun royal chairs atsakiyan falon, kujerune ƴan ubansu wanda aka narka kuɗi sosai wajen sayansu, asalin royal ne masu kyau da tsada, inda kalansu suka kasance milk colour and light sky blue sai kuma ratsin golding ash dake jiki,  sosai kujerun sukayi kyau, yayinda aka malale wani lallausan carpet mai taushin gaske a tsakiyan falon, wanda dazaran ka takashi ƙafafunka zasu nutse aciki saboda tsabar laushi,inda shima yake da kalar milk, and sky,   da wasu irin tsadaddun cottings aka ƙawata jikin window da kuma ƙofar falon, kalan cottings ɗin sun kasance ligh blue irin mai hasken nan,  sannan gaba ɗaya cottings ɗin simples suke basu da wani ado, sai ɗan ratsin golding ash kawai dake jikinsu, cotting ne masu azabar kyau da tsada, wanda suka ɗai ma sun isa ƙawata kyawun ɗakin,   can gefe kuwa wani irin ƙaton tv plasma ne wanda saboda tsabar girmansa yasanya ba'a kafasa ajikin bango ba, kan wani haɗaɗɗen table na glass aka ɗaurasa, wanda kalan table ɗin yakasance sky blue, sai kuma adon jikinsa daya kasance golding ash mai walwali,  gefe da gefen tv'n wasu irin haɗaɗɗun flowers aka sanya guda biyu, ƴan madaidaita, inda flowers ɗin suka kasance kowanne da kalansa, ɗaya milk ɗaya kuma sky, sosai haka ya ƙara ƙawata haɗuwan falon, can gefe kaɗan kuwa, rantsatstsen dinning area ne wanda aka ƙawatasa da haɗaɗɗen decoration mai masifar kyau, inda aka shirya wasu haɗaɗɗun royal chairs wanda suke kalan kujerun dake cikin falon saidai kuma yanayin tsarinsu baizo ɗaya ba, tsakiyan kujerun kuwa wani babban table aka sanya me masifar kyau,  gaba ɗaya falon walwali dake sheƙi yake inda yake fidda ƙyallin haɗuwa, sam ba acika shirgi acikin falon ba, komai antsarasa ne cikin nutsuwa da wayewa, sosai su Aunty Lubna ke yaba falon, saboda ko ƴar gwamna sai haka, sosai Yaya ahmad ya kashe maƙudan kuɗaɗe wajen sayan kayan furnitures ɗin, saboda yana matuƙar son Zaleeha taji daɗi ta zauna ɗakinta shiyasa zai iya kashe ko nawane akanta. Koda suka ƙarasa zuwa bedroom nansuka samu tuni angama shirya komai, inda acikin ɗakin ma aka zuba wani haɗaɗɗen furnitures mai azaban kyau,  don kuwa haɗaɗɗen royal bed mai kalan white and golding aka kafa mata, inda saman kan gadon ya kasance light blue colour,  sosai gadon ya tsaru da ado haɗi da ƙyale ƙyale irin na zamani, yanayin tsarin gadon kaɗai ya isa nusar dakai cewa ba ƙiran Nigeria bane, inda ajikin gadon akayi wasu haɗaɗɗun bedsite masu kyaun gaske,  gefe da gadon kaɗan kuwa wani tangamemen drawer ne wanda aka cika jikinsa da wani irin zanen ado mai masifar kyau haɗi da wani irin mirror glass me matsanancin kyau, kana can gefe kuwa wani haɗaɗɗen dressing mirror ne me kyaun gaske,  sai kuma stool ɗin sa wanda shima aka ƙawata jikinsa da ado mai ɗaukar hankali, again kuma wani dressing mirror ne ɗan madaidaici mai kyau aka aje aɗan gefe kaɗan,   tsananin tsaruwan da ɗakin yayi yasanya gaba ɗayansu suka shagala, tabbas ɗakin Zaleeha ya ƙawatu iya ƙawatuwa ko aturai al'barka,  komai dake cikin ɗakin abun so da burgewane, tabbas idan za a ƙiyasta kuɗin furnitures ɗin a iya ɗakima kaɗai banda parlour kayan sunkai na 4 million,  domin kuwa kayane masu masifar kyaun gaske,  haka suka dinga yaba kayan, koda suka buɗe bathroom kuwa mamakine yakusan kashesu, sosai aka ƙawatasa kamar ba bathroom ba,  inda wajen wanka ma na glass akayi mai masifar kyau wanda shi kaɗai ya isa ɗaukar hankalinka, sannan gefe ga wani haɗaɗɗen jakuzzie wanda aka ƙawatasa sosai, koda suka fito daga ɗakin na Zaleeha ɗayan ɗakin dake gefen nata suka shiga, don dama 2 bedrooms ne acikin falon,  shima sosai aka zuba masa wasu haɗaɗɗun furnitures masu kalan grey, sosai shima ɗakin yayi kyau, fitowa sukayi daga ɗakin inda suka ƙarasa zuwa cikin kitchine ɗin dake cikin falon, hmmmm wani kaya sai amale, anan fa haɗuwar take, komai dake cikin kitchine ɗin light pink and white colour ne,  sosai aka ƙawata kitchine ɗin, inda aka shirya komai na amfani acikinsa tsab,  da wasu zafafan food flask aka ƙawata jeren kitchine ɗin wanda aƙalla kowanni food flask ɗaya yakai 100k wato dubu ɗari, wani kamma harda ɗori, kaya masu kyau da inganci aka zuba acikin kitchine ɗin, tabbas Zaleeha kam anyi mata auren gata, Ya Ahmad da Baba Malam sun kashe mata kuɗi na fitan hankali wai duk dan su faranta mata rai ko sa samu ta zauna ɗakinta tayiwa mijinta biyayya,  haka dai suka dinga zagaya part ɗin suna yabawa da kyawun komai, inda Aunty Lubna ke ɗaukar komai awayarta, saboda haɗuwan kayan ya zarce misali. A sashin Saifuddeen ma a ranar aka shirya mishi sabbin kayan gadonshi masu masifar kyau, abundai sai wanda ya gani. Basu sukabar gidansu Saifuddeen ɗinba sai da sukayi sallan la'asar, bayan sun cika cikinsu da daddaɗan girkin Ummi, inda tayi musu haɗaɗɗiyar fried rice wanda yaji chicken, sai kuma kunun aya mai masifar daɗi,  ga kuma dambun kifi wanda yaji kayan ƙamshi, sosai sukaci abincin don yayi musu masifar daɗi, haka sukayi sallama da Ummi cikin girmamawa kana suka kamo hanyar dawowa gida. Itadai Zaleeha duk wannan wainar da ake toyawa babu idanunta aciki, don tun jiya takulle kanta aɗaki, bata fita koda cikin falo ne, hasalima zazzaɓi ne ke ɗawainiya da ita kwana biyun. A dare randa akaje akayi mata jeren ne, tayi mafarkin wai tana ɗakinta na gidan Saifuddeen ɗin tana zaune kan gadon, sai ta hango wani ƙaton maciji baƙiƙƙirin dashi yazo bakin ƙofar ɗakin nata yayi zuɗuɗuɗu ya shige ƙarƙashin gadonta, tana ganin har ya gama shiga ta kasa ihi ko neman taimako, saida taga binɗinshi ma ya shigene, sai kawai ta miƙe a guje ta fita daga ɗakin ta bar gidanma baki ɗaya, tanata gudu bata san inda zata jeba sai Mamanta da Bilkeesu da Ruda ta nuna mata bakin kogi, kawai sai ta nufi cikn kogin har ta fara nisa cikin ruwan da zai iya cinyeta sai taga wani farin dottijo bafulatani ya riƙo hannunta sun fita. To anan ta farka daga baccin kuma sai ta tashi da zazzafan ciwon kai. hakan yasa sam batason hayaniya. Musamman Mamy ta sa aka ɗauko mata ƙwararriyar mai zanen lalle da kitso don tazanawa Zaleehan, amma haka Zaleeha ta tubure tace sam ita babu wani lalle da za ayi mata, koda taga Mamy ta matsa kawai saita sa kuka, dan dole haka Mamy ta ƙyaleta, duk wani gyaran amarya kuwa dasuka shirya yi mata haka taƙi basu haɗin kai duk wani abun da za'a bata ace tasha ko taci sai ta buɗe musu shafin kuka, bisa dole suka ƙyaleta, itakuwa Zaleeha shawaran Bilkeesu ne ke yawo acikin ƙwaƙwalwarta, don kuwa Balkeesu ce tayi mata huɗuba akan kada ta yarda ta amince da komai na hidiman bikin, aure ne dai tabari a ɗaura idan yaso bayan an ɗaura auren an kaita gidan musakin plan ɗinsu da suka shirya zai soma aiki. Koda Rashida dasu Aunty Lumbna da Maryam a Mommy matar Malam Adam sukazo mata da zancen walima ƙi tayi fir taƙi yarda akayi ganin zata kunyatasu yasa suka shereta. Yau takama ranan jumma'a inda gobe take asabar wato ranan ɗaurin aure kenan, sosai su Saifuddeen suka shiga busy fiye dako yaushe,  hidiman ɗaurin auren na gobe kawai suketayi. Ɓangaren su Hayatuddeen da abokansa suma ba'abarsu a baya ba, don musamman suka ɗinka zafafan shaddodi wanda zasuyi fitan bikin dashi, inda Saifuddeen da kansa ya saya kowannensu haɗaɗɗen getzner wanda zasu saka wajen dinner inda kalan kayannasu ya kasance daban dana abokan ango. Tunda aka fara hidiman bikin har kawo yau Saifuddeen bai nemi Zaleeha ba koda awaya ne, duk wani abu na hidiman biki da  Rashida da Amira ƙanwar Ya Aminu a sauran ƙawayenta naa gari sukeyi don sunbasu haɗin kae sosai, Bilkeesu kuwa sai tsula rashin ɗa'a takeyi. Adaren na Jumma'a ne zazzaɓi mai zafi ya rufe Zaleeha, haka taƙi sanar da kowa saima ɓoye kanta da tayi inda ta duƙunƙune acikin bargo tana rawan sanyi, fatanta ɗaya shine Allah yasa ma zazzaɓin yazamo sanadin mutuwarta ta huta da baƙin cikin rayuwa. Ɓangaren Dalla kuwa aranan yaransa sukazo masa da labarin gano gidansu Zaleeha, harma da wajen aikinta, nan Dalla yacika da matsanancin murna, sai-dai kuma murnar tasa taso komawa alokacin da suka sanar dashi labarin aurenta da ake shirin ɗaurawa gobe, inda suka sanar masa cewar wani kurma kana gurgu zata aura, dariyan mugunta Dalla ya fashe dashi, inda yace.   "Ta kwana gidan sauƙi" nan yatsara irin rashin mutumcin da zaiyi mata,  nan ya ƙudurta aransa cewa dazaran an ɗaura mata aure da gurgun mijinnata ayayin da ake ƙoƙarin ɗaukan aure alokacin shikuma zaisa yaransa su ɗauko masa ita, tabbas shine zaisha wannan romon budurcin, al'ƙawari yaƴiwa kansa cewa saiyayi mata dalla-dalla tayanda bazata sake moruwaba. Saturday. 26/january/2019 Rana bata ƙarya. Ranan yau takasance wata muhimmiyar rana awajen Saifuddeen da duk wani mai ƙaunarsa, haka ranan tayau takasance wata rana wanda Zaleeha bazata taɓa mantawa da itaba a iyaka tsawon tarihin rayuwarta, ayau ne baƙin cikinta yafi na koyaushe ninkuwa acikin zuciyarta, ayaune takejin tsanan kanta da rayuwa fiye da kullum, ayau tanaji tana gani zata zama mata ga ga wani ba wanda ya taimaketa ba zata zama matar wancan mutumin da kyawawan manyan idanunshi ke bata tsoro. Federal lowcost. 9:30 am, gaba ɗaya gidan nasu acike yake da jama'a, ƴan uwa maza da mata haɗi da abokan ariziki, ko ina dake cikin gidan cike yake da mutane kowa ka gani fuskarsa ɗauke take da zallan farinciki. Can ɓangaren Saifudden nake jiyo hayaniyan mutane hakan yasa natafi don na duba meke tafiya acan, gaba ɗaya falon nasa cike yake da abokansa maza su, Ahmad, Jabeer, Ishaq, Saminu mijin Raihana, Wareesu, Saleesu, Mudassir, ibrahim, Rabi'u, Hisham, Jabeer da kuma abokanshi da sukayi karatu tare Hashim, Jafar,Abdulhakim. Gaddafi, Aziz da dai sauransu gaba ɗaƴansu sanye suke da tsadaddun shadda ƴan ubansu yayinda kowanne daga cikinsu yayi kyau sosai, gaba ɗayansu cike suke da farin ciki, domin dama ganin auren Saifuddeen ɗin shine cikar burinsu. dan duk da suna tare da taraddadin kar dai nakasar Saifuddeen tashiafi mazantakanshi to shiyasa ganin aurenshi shine burinsu. Ahankali yake murza wheellchair ɗinsa, inda ya ƙarasa zuwa gaban dressing mirror, cikin nutsuwa yake shafawa haɗaɗɗiyar surar jikinsa body lotion, koda ya kammala cumb ya ɗauka inda yashiga taje lallausan sumar dake kansa, wanda ya kwanta luf-luf kamar ƙawataccen sajen dake kwance akan fuskarsa, body spray ya fesa ajikinsa me daɗin ƙamshi, kana ya tura wheelchair ɗinsa zuwa kan gadonsa, inda anan ya aje kayan da zai sa. Cikin yanayi na nutsuwa da alamun gajiya da ɗan kazar-kazar ɗinshi kamar yanda ya saba ako da yaushe ya zura dogon wandon haɗaɗɗiyar getzner mai kalan white ajikinsa, yana gama saka wandon ya sanya rigar wacce ta kasance half jumper, cikin nutsuwa ya ɗauko babban garen kayan wanda aka yajiwa wani irin fitinannen aiki da surfani blue colour mai masifar kyau, cikin nutsuwa ya zurata akan rigar tasa, lokaci ɗaya yayi wani irin azababben kyau mai tafiya da zuciya, ahankali ya zura wasu haɗaɗɗun toms ƙiran Italy aƙafafunsa masu azabar kyau da tsada, yayinda takalman suka kasance blue colour, wato kalan aikin garen jikinsa kenan, wasu tsadaddun links masu tsadan gaske yasanya ahannuwan rigar, kana yaciro wani tsadadden wrist watch mai tsananin kyau da tsada daga cikin wani ɗan ƙaramin box, agogon rolex ne me masifar kyau, ɗaura agogon yayi ahannunsa na dama tare da ɗaukan haɗaɗɗiyar hulansa mai tsada wacce take da kalan blue ajikinta yasanya, tare da dai-dai-ta zamanta akansa. Tabarakallahu ahasanul khaliƙiyn! wani irin fitinannen kyau Saifudeen yayi wanda tunda yake bai taɓayin irinsa ba, gawani azababben kwarjini da yayi, wani irin ƙyalli da walwali fuskarsa keyi, sajen nan nashi yayi lib-lib akan farar fatar kekyawar fuskarshi, jajayen laɓɓansa sai sheƙi sukeyi tamkar ya shafa musu mai, gashin girarshin nan ya kwanta lib gwanin ban sha'awa, yayinda getzener ɗin jikinsa kuwa keta shinning, getzner ne me masifar tsada da kyau, wanda aƙalla kuɗinta yakai 95k, sosai kuma kayan suka amshi jikinsa. cikin nutsuwa ya ƙarasa gaban dressing mirror, kallon kansa yayi acikin madubin tare da sakin murmushi, shi kansa ya aminta da kyawu haɗi da cikar halittan da Allah yayi masa, shiyasa akullum yake gode masa, tabbas Allah abun godiya ne, sam bazai iya fasalta matsanancin farin cikin dayakejin kansa aciki ba, yau zuciyarsa zata samu cikar muradinta, wani haɗaɗɗen parfumed mai ƙamshi ya fesa. Kana ahankali ya danna madannin kekensa, kaitsaye ya nufi hanyar fita daga cikin ɗakin, buɗe ƙofar yayi ya fito ahankali, idanu su Ahmad suka zuba masa, baƙaramin kyau yayi ba, wanda sukansu maza ƴan uwansa sun ƙyasa da gayun nasa inaga mata kuma? sosai suka shiga yaba tsantsar kyawun nasa, inda Ishaq keta tsokanansa, shidai Saifuddeen sai murmushi kawai yakeyi don kuwa yau yana cikin farin ciki, nanfa dukansu suka shiga yi masa hoto, bayan sun gama yi masa hotonne kuma suka shiga ɗaukan selfie dashi, inda sukayi kyau sosai, zuwa lokacin ƙarfe 10 har da kusan rabi tayi hakan yasa suka ɗunguma sukai waje, don kuwa ƙarfe 11 dai-dai ne za a ɗaura auren. A falon Ummi kuwa tana ganin fitowansu ta ratso gefe tana zuwa Adda Rahma da Raihana da Raliya suka biyo bayanta, kanshi ta dafa tare da cewa. "Allah ya bada sa'a Babana , yau kayi kyau sosai irin kyan da ban taɓa ganin kayiba." Amin Amin sukace baki ɗanyansu, shi kuwa Saifuddeen alama ya mata da ya gode, su Adda Rahama kuwa selfie suketayi dashi. gannin zasu ɓata lokacine Salisu yace. "Adda Rahma ku barmu mutafi". to tace kana suka barsu. Acan compound ɗin gidan kuwa su Hayatudden da abokansa ne tsaye, sosai matasan yaran sukayi kyau cikin shigarsu ta shadda sky blue wanda yayi masifar amsarsu, dukansu cike suke da farin ciki inda suketa ɗaukan hoto da sabuwar wayar ta Hayatudden iphone 7+ wanda Saifuddeen ne ya saya masa, fitowar su Saifuddeen yasa dukansu suka maida hankalinsu garesu, tuni Hayatuddeen ya shiga santin irin kyawun da Hamman nasa yayi, nan yashiga ɗaukan Hamman nasa hoto, daga bisani kuma yashiga yi musu selfie. Cikin yanayi naɗan sauri sauri kowanne ya nufi mota don kuwa lokaci nata ƙurewa, wata zazzafar RANGE ROVER black colour sabuwa dal mai azabar kyau da sheƙi da ƙyalli Saifuddeen ya shiga, wanda musamman ya sayeta saboda da ita yakeson yin hidiman biki, Ishaq ne yashiga gefensa ya zauna, su Ahmad kuwa kowa motarsa ya shiga hakama sauran abokansa baki ɗaya dan babu ƙaranta, yayinda aka warewa Hayatuddeen da abokansa motarsu guda ɗaya zazzafa wanda suma da ita zasuyi chilling ɗinsu wajen bik. su Baffa Ali da Malam Ashiru kuwa wata haɗaɗɗiyar mota ƙiran mercedes suka shiga don sune suke matsayin iyayen ango, Dirankaɗi ma yazo da abokansa, inda su Alhaji Khabeer da Alhaji Ibrahim, haɗi da Alhaji Ishaq Ba miskila, San Husssain Alhaji Yawale Alhaji Aliyu mai dilan leda Malam Habu dama sauran manyan ya kasuwa duka Ya Rabi'u ma yayan Ishaq na Abuja yazo haka Dr Aliyu .Ya Adnan da abokan shi hakama bappa Ali da abokanshi da abokan Abbansu Saifuddeen suma sunzo don halartan ɗaurin auren, gaba ɗaya haka motocinsu sama da talatin da biyar suna jera reras akan titi line by line haka suke tafiya cikin nutsuwa. Duk inda jeren motocin suka wuce sai anbisu da kallo ahaka har suka isa cikin unguwar NEW G.R.A, can gefe sukayi parking motocinsu, don kuwa ƙofar gidan su Zaleeha cike yake da mutane maƙil, manyan malamai, manyan ƴan kasuwa, da kuma ƴan siyasa duk sun samu zuwa ɗaurin auren, saboda Baba Malam mutum ne da sunansa ke yawo acikin Nigeria, kusan kowa ya sanshi, kana ga Yaya Ahmad da sanadinshi yasa pilot suka rinƙa dirowa birnin gombe da jiragensu dan halartan ɗaurin auren ga kuma sojojin da ys Aminu suma sun gayyato nasu mutanen. Raveel ma ya gayyato duk abokan aikinsu. Isowar su Saifuddeen yasanya gaba ɗaya kallo ya dawo kansu, kowa kallon Saifuddeen yakeyi, wanda nagarta haɗi da haiba da kwarjini da kamalarsa ya cika idanun mutane, sam basai an faɗa maka ba da kallonsa zakagane cewa shine angon, sai-dai kuma da yawa suna mamakin kasancewarsa gurgu. Cikin mutunta juna Baba Malam da tawagarsa suka amshi su Saifuddeen, kamar yanda lokaci baya jinkiri wajen zuwa 11:00 am dai-dai dubbanin jama'a suka shaida ɗaurin auren SAIFUDDEEN Muhammad Ahamad Dukku da kuma ZALEEHA Bashir Sulamain Dukku akan sadaki naira dubu ɗari...! Littafina na kuɗine duk wanda ya fiddamin shi aradun Allah yaseeeeeeeen doooooooguwa buluƙutu baƙar mutuwa! *BY* *GARKUWAN FULANI* [9/9, 9:05 PM] +234 806 222 4030: _Shafinga ƙyauta ne gareke babana, Ali Wambai, inai maka fatan al'khairi a rayuwarka, yaro mai sunan manya Allah yasa ka samu nagarta irin na masu sunan naka_ A hankali ya lumshe Kyawawan idanunshi, tare da furta. "Masha Allah!." a cikin zuciyarshi sosai tayi masa kyau acikin shigar wedding gown ɗin nata, har wani ƙyallin kyau take kamar wata tauraruwa, komai nata yazama wani na musamman,  cikin nutsuwa haɗi dajan aji irin na amare suka ƙaraso wajen motar Saifuddeen ɗin, da sauri Sule driver ya ƙaraso inda ya buɗe murfin motar da kansa, idanunta dake cikin wani ɗan siririn mayafi ta rumtse sakamakon ƙamshinsa da yadaki hancinta, sakamakon buɗe marfin motar da akayi, da taimakon Balkeesu tashiga cikin motar, ƙasa-ƙasa Balkeesu ke kallon Saifuddeen, sosai yayi bala'in yin kyau, saikace wani balarabe, komai nasa is perfect, sosai Saifuddeen ya haɗu, haƙiƙa musamman a irin wannan rana ko maƙiyinsa bai isa kushesa ba. Zaleeha na gama shiga cikin motar Sule driver ya maida murfin motar ya rufe. wata muguwar hararan Balkeesu ta abkawa Sule driver, cikin takaici tabi Rasheeda suka shiga wata mota ta daban. Ahankali Sule driver ke tafiya dasu acikin motar,   idanu Saifuddeen ya lumshe tare da jingina bayansa da jikin kujeran motar, sosai yake shaƙan daddaɗan ƙamshinta, hakanan haɗewar ƙamshin turarensa da nata  suka ba da wani irin yanayi me daɗin gaske, irin yanayin ƙamshin nan mai sauƙar da kasala uwa uba ga sanyi Ac da motar ke busa musu,    cikin nutsuwa ya ɗaura hannunsa ɗaya akan nata hannun, take haɗuwar lallausan fatar jikinsu waje ɗaya ya ƙara sauƙar masa da kasala, cikin ƙunan rai da hatsala Zaleeha tayi yunƙurin janye hannunta baya, amman sai ta gaza hakan jin ya rumtse tafin hannunta cikin nashi sosai zuciyarta ke tafasa, gefe guda kuwa ga ƙamshin turarensa wanda gaba ɗaya yabi ya cika mata hanci yana birkita mata kwanya sai shaƙar daddaɗan ƙamshin nashi takeyi, wanda tsabar tsanan da tayiwa mai turaren yasa take ta son cusawa ranta tsanan ƙamshin turaren nasa har wani abu me ɗaci-ɗaci take rayawa kanta takeji acikin maƙoshinta, zuwa yanzu har rasa yanda zata misalta tsanarsa aranta takeyi,  komai bayayi mata daɗi, tana daurewa ne kawai don plant ɗinsu da suka shirya yakai ga ci, ga kuma gargaɗin ya Habu wanda tasan ba mitunci ne dashi ba, bacin haka babu wani abu da zaisanyata zuwa wannan banzan diner'n toma da wanne angon zata taka ta shiga. Ganin tajanye hannunta daga cikin nasa yasanyashi maida kansa jikin lallausan kujeran motar, numfashi yake fitarwa ahankali, yayinda wani irin kasala ke sake lulluɓe masa jiki. Kowannensu zuciyarsa ɗauke take da tunani kala-kala shi ji da gani yake kamar bata tsiraba daga sharrin masu son saceta da haryanzu hidimar bikin bata barshi ya gama bincikosu ba, ita kuwa ji take da zama kusa dashi gwara zama kusa da bakin kura. A haka suka ƙaraso babban wajen wanda aka ƙawatasa iya ƙawatuwa, wato Gombe International Hotel, sosai wajen ya haɗu komai gwanin burgewa ga kuma tsaron da dole yasa yaran Dalla barin wurin. Acan cikin babban hall din da za'a gudanar da diner ɗin kuwa, kowa zuwan ango da amarya kawai yake jira,  gaba ɗaya mutanen dake wajen zuciyarsu awanke take da farinciki, yayin dasu Hayatuddeen keta ɗaukan pictures, suma zuwan ango da amarya kawai suke jira kafun nan abasu filin cashewa, don al'ƙawarine yau sai gaba ɗayansu sunnu nawa Hamma Saifuddeen ɗin gata, wannan rana itace ranan da Hayatuddeen dakuma gaba ɗaya dangin da abokan Saifuddeen ke jira, hakan yasa suke fata da burin faranta ran ɗan uwannasu tahanyar ƙawata masa bikin nasa yanda zaiyi armashi. Labarin isowar ango da amarya da MC yajine yasanyashi soma labartawa jama'an wajen cewa. "Allah yayiwa ango da amarya isowa." Nanfa kowa ya zubawa ƙofar hall ɗin ido, gaba ɗaya mutanen wajen sun zaƙu dason ganin amarya da angon. Ishaq wanda yasha dakakkiyar shaddarsa blue tare da wani haɗaɗɗen glass, wanda idan baka san shiba bazaka taɓa shaida cewa makaho bane, don kuwa komai nasa irin na masu gani yakeyi,  Ishaq da kuma Ahmad haɗi da Hisham da kuma Aziz wanda yana ɗaya daga cikin abokan Saifuddeen wanda sukayi Gombe State University tare sune suka fita don zuwa taro ango da amarya, wanda dama tuni su Balkeesu da Rashida suna da ƙannan Ya Aminu yaran Yayan Baba malam da yara Goggo Maryam da dai sauran ƴan uwan amarya waje, don kuwa sune suka riƙewa amarya Zaleeha ƙasan rigarta dake da matsanancin tsawo, wanda dole ya zama sai an riƙe mata shi. Sule driver ne ya ya buɗewa Saifuddeen ƙofar motar tare da ware masa sabuwar kekensa mai azabar kyau, har wani ɗauke ido da ƙyallinta keyi Cikin azama da alamun iya sarrafa kai da cikar nitsuwa ya hawa kan keken Saifuddeen ya dai-daita zamanshi hakan kuwa sai yayi bala'in ƙarawa kwalliyar tasa armashi, don kuwa wani irin kwarjini ne yasake bayyana atattare dashi, zamansa akan  wheelchair ɗin nasa sai ya ƙara masa girma da wani irin kima, ya fito tamkar jinin sarauta sule driver ne ya buɗewa Zaleeha murfin motar, ahankali ta zuro da kyawawan ƙafafunta wanda sukaji tsadaddun takalma masu kalan pitch,  tana gama fitowa daga cikin motar, su Rasheeda suka tattaro ƙasan rigar nata inda suka riƙe mata shi, ahankali Saifuddeen ya danna madannin wheelchair ɗin, take yasoma tafiya dashi, cikin nutsuwa yaƙaraso inda Zaleehan ke tsaye, kasan ceqarshi dogo, kuma wheelchair ɗin yafi sauran tudu, kana tanada maddan da za'a ƙara tunda ko a rage sai ya zama yayi tsawo in ka hankosu zakayi zaton a tsaye yake hannunshi yasa ya kamo nata ya ɗan haɗe tafukan hannunsu ya rumtse. Ahankali suka soma takawa inda yake sarrafa wheelchair ɗinsa cikin nutsuwa, wani irin haɗuwa da burgewa tsarin tafiyan tasu ya bada, duk dacewa shi yanakan wheelchair ne, amma kuma sai hakan yaƙarawa kwalliyar tasu armashi, don kuwa zamansa akan wheelchair'n ya bayyana tsantsar ajinsa da kuma kwarjininsa da kima da kamala uwa uba ƙasaita, hakan yasa mutane da yawa zasuyi masa kallon zallan ajine da kasaita yasanyashi naɗewa akan kujeran, wanda saima ka lura sosai zaka iya gane cewa wheelchair ne don kuwa kujera ce mai tsananin tsadan gaske, musamman aka kawo masa ita daga Germany. Ishaq da Ahamad ne ke biye dasu, saikuma su Rashida dake riƙe da jelan rigarta, bayansu kuwa Aziz da wasu matasa wanda sune zasu bada tsoro a wurun dan yanzuma akwai mashunan UD da suke zargi a wurin. Jabeer ne da kuma Hisham ke biye dasu Ahmad ɗin a baya, sosai tsarin nasu yayi kyau,  cikin nutsuwa suka kutso kansu cikin hall ɗin. Lokaci guda mutane suka somayin hanmdala sakamakon ganinsu, dan sunyi bala'in burgesu, nanfa Diamond Photograpgy suka soma aikinsu na ɗaukan hoto, sosai akeyi musu hoto, ga wani sassanya kiɗa dake tashi. Ahmad da ishaq da Salisu da Aziz kuwa da yayyafin kuɗi suka biyo bayan ango da amrya, yayinda rashida kuwa ke fesa wani abu mai ɗan karen ƙamshi kana yana bada kalan wal-wali. ɗaukansu hotuna tako ina, don sun bala'in yin kyau da dacewa, yanayin yanda Saifuddeen ke hakimce akan kujeransa shiya ƙara zautar da mutane, don hakan ya masifar ɗago ajinsa, sosai yayiwa kowa kwarjini, take ƴan matan da suka samu halartan wajen diner'n suka mato akansa, sosai dayawan mutane ke hamdala da godewa Allah, don kuwa tabbas Saifuddeen ya cika cikakken namiji kuma ingarma, maiji da tashen kyau haɗi da kwarjini,  haka kuma mutane da yawa ke yaba tsananin kyawun da amarya Zaleeha tayi, don kuwa kowa na iya hango beauty face ɗinta ta cikin wani ɗan abun da aka ɗiga mata akanta wanda yaɗan rufe gefen fuskarta kaɗan, sosai su Adda Rahama ke yaba kyawu da haɗuwar Zaleeha, tabbas sai yanzu suka tabbatar da cewa bawai abanza Saifuddeen ya nace akan cewa sai ita ba, haƙiƙa Zaleeha tacika mace abunso ga kowani irin ɗa namiji, sannan kyawunta ya isa kyau,  sosai kowa yaga dacewarsu da Saifuddeen ɗin, don kuwa kyaune ya gauraya da kyau. Wani irin cool music  na Ed sheeran mc ya sakar musu irin mai taɓa zuciyar nan, hakanne ya ƙara bawa tafiyar da sukeyi armashi,  Hayatuddeen da abokansa ne suka zo sunayi musu live vedio,  Ahaka har suka ƙarasa wajen da aka ƙawata domin zaman ango da amarya, wajene wanda aka ƙawatasa da decoration mai kyaun gaske, wanda akayi amfani da colours irin na kayan dake jikin ango da amarya,  cikin nutsuwa Saifuddeen yayunƙura ya sauƙa daga kan kekensa cikin nutsuwa haɗi da salon mai armashi ya hau kan wata rantsatstsiyar royal chair wanda tagaji da haɗuwa,  Rasheeda ne ta zaunar da Zaleeha agab dashi har takai ga jikinsu naɗan gogan na juna. Kamar yanda aka saba ango da amarya na zuwa wajen diner ake fara gudanar da shagulgula hakanne yasanya babu wani ɓata lokaci MC yabuƙaci da babban abokin ango akan yazo yaɗan basu biography na ango. Ishaq wanda fuskarsa ke ɗauke da murmushine yataso inda ya ratsa cikin yawan jama'an tamkar wanda yake gani haka yaƙarasa gaban MC, mike  ya karɓa inda yayi gyaran murya, cikin nutsuwa haɗi da kamala yasoma bada ɗan taƙaitaccen tarihin Saifuddeen ɗin, sosai biography'n na Saifuddeen ya taɓa zuciyar kusan gaba ɗaya mutane dake wajen, duk da cewa in brief Ishaq ɗin yayi komai, amma tabbas rayuwar Saifuddeen cike take da al'amura masu sosa zuciya, dayawan mutanen da basusan Saifuddeen ɗin ba, sai alokacinne ma suka san da cewa shiɗin kurmane, koda Ishaq yagama bada ɗan taƙaitaccen tarihin na saifuddeen, take jama'an wajen suka soma tafi,  sosai aka jinjina gwarzantaka irin na Saifuddeen don haƙiƙa yacika Namiji. Ishaq na komawa, still Mc yasake buƙatan babbar ƙawar amarya don tazo ta bada biography na amarya. Tsulum Balkeesu tasoma ƙoƙarin miƙewa zuciyarta cike da mugunta, don kuwa dama tuni tagama kitsa kalaman da zata faɗa agame da amaryan, haka kuma tashirya gasawa Ango magana afakaice, saidai kafun ta farga  sai tsintar muryar Rasheeda tayi acikin kunnuwanta, wanda sanin halin Balkeesun da mugun nufinta ne yasanya Rasheeda rigata zuwa, don tabbas tasan balallai abun da Balkeesu zata  faɗa yazamanto al'khairi ba, wannan ranan kuwa ta farinciki ce, sam batason aɓata ran kowa, sudai da suka ɗaukawa kansu dala ba gammo sai suyita fama. Cikin nutsuwa Rasheeda ta ɗan bada taƙaitaccen tarihin Zaleeha, wanda kuma iya abun da ta sani ta faɗa, nan mutane da yawa suka ƙara gaskata cewa lallai Amaryar Saifuddeen ɗin ƴar ƙwalisa ce, don aɗan biography ɗinnata da Rasheeda ta bayar, zaka fahimci cewa, itaɗin ƴar ƙwalisa ce, sannan mai aji da kuma wayewa, uwa uba ƴar gidan hutu ce, sam bata wani san baƙin cikin rayuwa ba kuma ƴar gidan mutunci ce. Koda aka gama gudanar da biograpy nanfa mc yasake musu music mai daɗi da taɓa zuciya,  inda aka ɗan soma ƴan ciye ciye wanda aka kashe maƙudan kuɗaɗe wajen tsara abunci dana sha. Haka suka shiga gudanar da diner ɗin cikin nutsuwa, bayan ankammala ciye ciye ne, mc ya sanya wata waƙa mai daɗin gaske, nanfa ya buƙaci da ƴan uwa suzo don nunawa amarya da ango ƙauna. Aunty Rahama, Raleeya, da kuma Raihana, Aunty Kubra sune wanda suka fara miƙewa tsaye, don filin nasune na musamman,  cikin yanayin taku haɗi da ɗan rawa mai burgewa suka ƙarasa kan step ɗin da ango da amarya suke,  sosai suka burge kowa musamman shigar alfarman dake jikinsu tunkan su ƙaraso Saifuddeen ya miƙowa Adda Rahama hannunsa, cikin nutsuwa Adda Rahama takamo hannun nasa ta riƙe tana murmushi, hannu tasa ta shafi gefen fuskarsa take ta buɗe wata ƴar purse ɗinta, fararen ƴan dubu-dubu miƙaƙƙune suka cika cikin jakan,  haka suma su Raihana da Raleeya da Aunty Kubra gaba ɗayansu jakakkunansu suka buɗe, kuɗaɗen suka ciro inda suka soma yiwa ɗan uwannasu da amaryarsa ɓarinsu, kuɗi suke zuba musu sosai har kaman basason kuɗin, yayinda wajen ya cika da kiɗa haka masu vedio da kuma photo sunatayi, abun sosai yake ƙayatarwa, shikansa Saifuddeen saida yasha mamakin yanda ƴan uwannasa ke ɓarar da kuɗi wajen yi masa liƙi, suna cikin yi musu liƙinne, Dr Adnan da kuma Ahmad, haɗi da Saminu da General Abbas mijin Aunty Kubra suka ƙaraso. Hohoho idan bakwayi kuban waje, domin kuwa sosai suka shiga taya matansu likin, nanfa abun yaƙara girmama mutane da yawa sai sakin baki sukayi suna kallonsu, Ahmad kuwa har kamo Raleeya yake suna ɗan taka rawa atare, sosai suka nunawa Saifuddeen ɗin ƙauna, kafun daga bisani mazajensu suka janyesu inda sukabar kan dandamalin,  nanfa mc yabawa gaba ɗaya abokan ango dama. Nanfa akeyinta rigiji rabgi , domin kuwa gaba ɗayansu da rawa suka shigo cikin filin, hakanne yasa gaba ɗaya hall ɗin aka ɗau sowa, don sosai abun ya ƙayatar, babuma kamar ishaq, Aziz, Ahmad, Salisu, Warisu tumbuleƙe, Mudassir, Jabeer, Hisham, kai baki ɗayansu dai wanda suke rawa sosai, babu wani kunya ko ɗar, acewarsu ranan da suke jirane tazo, Ibrahim, Wareesu, Saleesu, Saminu, da kuma Aziz da sauran school friend ɗin Saifuddeen ɗin kuwa suma sosai suka taka,  Ishaq ma da ba gani yake ba haka ya gwada basirarsa wanda ya burge kowa,  Ahmad ne ya jawo Saifuddeen zuwa cikinsu, har tsakiyarsu ya jawosa bisa kan wheelchair ɗinsa,  nanfa suka kewayesa sukayi mishi zube suna rawa tare dayiwa junansu ɓarin kuɗi, ko ina dake cikin hall ɗin tafi haɗi da shewane ke tashi, domin sosai salon na abokan Saifuddeen ya tafi da kowa, sun bala'in burgewa. Koda suka gama bidirinsu suka koma, nanfa mc yayi gyaran murya tare da ƙiran masu gayya da aiki, ginshiƙai kuma ƙannen ango. Hohoho inji hausawa sukace abu namu maganin akwaɓemu. Su Hayatuddeen da Zakariyya Imran da Sulaiman kana isma'il da Faruq ɗan Adda Rahma. Manyan ƙanne, yara matasa masuji da ƙarfi ajikinsu, ƴan matasan da suke ji da tashen tasowarsu, salon rawar tasuma ta dabance don kuwa saida ango da kansa yashiga tafa musu, don da wani irin ƙayataccen rawa suka shigo cikin filin, nanfa aka somayi musu ihu ana ƙara zugasu kansu na ƙara girma, harta Isma'el ɗan Alhji Kaburu dayake kurma saida ya taka,  sosai Hayatuddeen da abokansa Imran, Sulaiman, Isma'il da ƙanin amarya Zakariyya rawa irin ta zamani sukeyi mai ɗaukar hankali, hakanan jama'an wajen sukaji kwaɗayin yi musu liƙi, don kuwa rawan nasu yayi kyau sosai, nanfa jama'a suka soma yi musu ɓarin kuɗin. Ango Saifuddeen kuwa sai wani ƙasaitaccen murmurshi yaketayi hannunshi rike da hannun Zaleeha daketa mutsutsun kwacewa, yayinda hawaye ke zubo mata tabbas taron ya haɗu iya haɗuwa irin haɗuwa na kece raini da nunawa sa'a taso ace da wanda take sone take zaune a yanzu ,domin har tsikar jikinta tashi yakeyi yadda hall ɗin ya ricaɓe aketa ɓarin kuɗi, ita da kanta tasan babu ƙaranta a bikin ta kuma yarda komai na alfarma akeyi ta gamsu da ranta mijinta kuma kekyawane irin kyau na kece raini da nunawa sa'a ta kuma gamsu mai cikekkiyar tsabta ne da gayu, kuma masoyine na gaskiya dan taga salon zazzafar soyayyarshi to amman mijinfa bashi da maraba da ginennen taɓo kuma duk haka tasan yazo a ƙirerren lokacine wlh da yazo kafin haɗuwanta da wanda ya taimaketa tabbas yanada nagartar da dole ta soshi to amman a makere yazo, kuma sai takeji can cikin zuciyarta kamar wani abu ke sarrafa mata zuciya, bata dawo daga duniyar tunaniba taji sauƙan tattausan yatsunshi kan haɓarta da sauri ta ɗan juyo ta kalleshi sai kuma tayi maza ta lumshe idanunta ganin ya ɗaga mata girarshi ɗaya tare da kashe mata ido kana ya ɗan kaɗa mata harshe alamun, ya dai, kana ya ɗan nago hannunta dake tsarke da nashi bayan hannun nata ya juya tare da manna mata wani irin sassanyan kiss. wow nanfa masu hoto suka koma kansu. Cikin farinciki Hayatuddeen yaƙarasa wajen Hammansa nanfa yasanja salon rawarsa, hannun Hamman nasa ya kamo, ahankali yake juya kujeran Hamma Saifuddeen ɗin nasa, hakan yasa abun yaƙara armashi, murmushin farinciki kawai Saifuddeen ɗin keyi, haƙiƙa ƴan uwa da abokansa sun nuna masa tsananin gata, nanfa Hayatuddeen da abokansa suka ciro kuɗaɗen al'jihunsu suka soma zubawa Saifuddeen da Amarya Zaleeha, Zakariyyane yaƙarasa jikin ƴar uwartasa ahankali ya kamo hannuwanta tare da jawota tsakiyan filin, tayi matuƙar mmkin ganin Ya Aminu Ya Ahmad Ya Habu Aunty Shatu Aunty Lubna da Adda Maryam dasu Amira ƙannen ya Aminu sun mata zobe ita da ango Saifuddeen suna mata yayyafin kuɗi, Zakariyya kuwa nan ya riƙe duka hannuwanta, cikin tsananin ƙaunar ƴar uwartasa yasoma ɗan jijjigata hakanne yasa Zaleeha taɗan saki murmushi, nan taɗan soma ƙafafunta, ganin haka yasa gaba ɗaya su Hayatuddeen suka ke wayeta suna rawa, bisa dole Zaleeha ta biyesu suka ɗan soma takawa,don kuwa ansanya musu wata daddaɗan waƙa, wanda ko baka da niyar yin rawa saika taka, bare ita Zaleeha uwar son waƙa da kiɗi haka yasa taɗan saki jikinta bayan anyi musu ɓarin kuɗi sosai takoma kan kujeran ta zauna tana me maida ajiyar zuciya. Haka dai akayita shagulgula masu ƙayatarwa yan ƙungiyar jonapwd sunyi matuƙar bada mmkin irin kuɗaɗen da suka liƙawa ango, nairori kam awannan rana sunyi kuka sosai, an ɓarnatar dasu baɗan kaɗan ba, sai wajen ƙarfe 10:00 pm, aka kammala gudanar da diner'n, nan kowa yasoma ƙoƙarin tafiya gida, don dayawan mutane amatuƙar gajiye suke, babuma kamar Saifuddeen, wanda dama shi sam bai iya jure wahala, abu kaɗan ke gajiyar dashi, sai yaji duk yazama very weak bare kuma ga hidimar da yasha, yanzuma babu wani abu dayake buri da fatan gani kamar Umminsa, so kawai yake yaje yayi mata complain ɗin gajiyar dake damunsa, kamar yanda sukazo amota ɗaya haka komawarsu ma takasance amota ɗaya, saidai har suka iso gidan ko ƙala baice mata ba, gaba ɗaya gajiya ke damunsa, itama Zaleehan agajiye take hakan yasa ta lafe jikinta ajikin kujeran motar tare da lumshe idanunta da suke cike da bacci. Jin isowarsu yasanya dakanta ta buɗe murfin motar ta fice, ko tsayawa batayi ba, riganta na sharan ƙasa haka tanufi ɓangaren nasu, don ta zaƙu da ta cire rigan, sam bata wani iya zama da kaya mai nauyi ba, musamman ma wannan dayake wedding gown. Shima Saifuddeen saita wheelchair dinsa yayi tare da hawa kai, kaitsaye yanufi cikin gidan nasu. Kasancewar darene babu wani hayaniya, dayawan mutane bacci suke, waƴanda suka dawo daga wajen diner kuwa tuni kowa ya shige ɗaki don ya ɗan huta,  ahankali yake tura wheelchair ɗinnasa har yaƙaraso cikin falon, idanunsa ne sukayi masa tozali da Umminsa dake zaune acikin falon, yana ganinta yaɗan lumshe idanunsa tare da shagwaɓe fuska, murmushi Ummi tayi tare dayi masa duban tsab, tabbas tasan da cewa Saifuddeen bazai taɓa dawowa har ya kwanta  batare daya neme ta ba, tasan dolene zaizo gareta hakanne ma yasa tazauna afalon zaman jiransa, ahankali ya ƙaraso tare da ɗaura kansa akan kafaɗan Ummin, cikin yanayi na zallan shagwaɓa ya ɓata fuska tare da taɓe red colour lips ɗinsa. Hannu Ummi tasa tashafi lallausan sumar kansa, cikin kulawa tace. "Ka gaji ko?." Kansa yajinjina mata alamar "Eh." Tare da ƙara maida kansa jikinta, tamkar wani yaro ɗan shekara shida haka ya koma mata, sakalci haɗi da shagwaɓa kawai yake zuba mata, komai ta cikin body language ɗinsa yakeyi mata,  sosai Ummin ke lallaɓinsa, sarai dama tasan ɗanta bayason wahala, gashi da ɗanbanzan shagwaɓa, abu kaɗan ke wahalar dashi sai dai jarumtar zuciyarshi na danne sakalcinsa, lallaɓasa Ummi tayi tare da cewa. Yaje yayi wanka, tun tuni dama tasa anshirya musu abinci akan dinning area. Da ƙyar Ummi ta iya lallaɓasa yabar part ɗin nata, yana fita yasamu su Ahmad da su Ishaq wai zasuyi masa rakiya zuwa wajen amarya, nanfa yace musu ya gode, ganin cewa dama suma sungaji yasa suma basu matsaba, nan kowa yanemi inda zai huce gajiyarsa, Ahmad da Saminu kuwa kowa matarsa ya kama suka ƙule aɗaki. Cikin nutsuwa Saifuddeen ya kutsa cikin ɓangaren nasu, babu kowa acikin falon sai daddaɗan ƙamshin turaren wuta, dubansa yakai ga ƙofar bedroom ɗin na Zaleeha, nan yagansa agarƙame, baiwani damu ba yanufi ƙofar dazata kaisa zuwa falonsa, don kuwa  dole sai yabi ta falon Zaleehan kafun yasamu kansa cikin nasa falon. Yana shiga haɗaɗɗen falon nasa kai tsaye ɗaki ya nufa, kayan jikinsa ya shiga ragewa, saida ya rage dagashi sai gajeren wando sannan ya nufi toilet, shida kansa ya haɗawa kansa hot water acikin bathtube, kwanciya yayi lub aciki tare da lumshe idanunsa, sosai yaji daɗin ruwan don ahankali yaɗanji gajiyan jikinsa naɗan warwarewa,  wanka yayi insa ya fito daga cikin bathroom ɗin bayan ya ɗauro alwala, koda ya fito wata marroon ɗin jallabiya ya sanya, duk da akwai gajiya ajikinsa ko kaɗan hakan bai hanasa yin sallah raka'a biyu ba yana idarwa ya shafa addu'oinsa sannan yabi lafiyar gado, light off na wutan ɗakin yayi tare da jawo blanket ya rufa ajikinsa, lumshe idanunsa yayi, sannu ahankali tunanin matarsa ke mamaye zuciyarsa,  ahaka bacci mai nauyi ya ɗaukesa. Washegari Ƙiran sallan asuban fari ya farka, nan yatashi tare da faɗawa bathroom yayi wanka haɗi da ɗauro alwala, koda yafito dogon wandon jeans da kuma white crazy shirt yasanya ajikinsa, sosai kayan sukayi masa kyau, kan kekensa ya hau inda ahankali ya buɗe ƙofar ɗakin ya fice. Cikin nutsuwa yake tafiya da keken nasa har yakawo cikin falon na Zaleehan, ɗan shiru yayi ganin wutan ɗakin a kunne da kuma alamun motsi acikin ɗakin nata yasa kansa tsaye yafice daga cikin falon, don ya tabbatar da cewa tatashi sallan asuba ne. Direct masallacin dake gefen gidannasu ya nufa. Zaleeha kuwa fitsarine ya tasheta koda taga lokacin sallan asuba yayi kuwa shine taɗauro alwala, nan tazo tayiwa Zaheera dake kwance akan doguwar kujeran dake cikin ɗakin tashin duniya amma Zaheera taki tashi, sabida gajiyan hidimr daren jiyan hakan yasa dole Zaleeha ta ƙyaleta, nan ta shumfuɗa sallaya inda ta tayar da sallah,  tana idarwa ta soma gabatar da azkar ɗinta, koda ta gama, wayarta ta jawo inda ta shiga Qur'an app nan ta buɗe suratul baƙara ahankali cikin zuciyarya take karatun sai dai tana farawa kasala da wani gyangyaɗi mara tushe ya rufeta ta rasa meyasa haka cikin kwanakin nan duk sanda zatayi niyar yin karatu sai taji wannan yanayi da kyar take iya farawa dai. Ɓangaren Saifuddeen ma kuwa tunda yayi sallan Asuba yana nan zaune acikin masallacin, karatun Al'Qur'ani yayi sai 7 dai-dai yabar cikin masallacin, kaitsaye ɓangaren Umminsa ya nufa, dan zuwa gaisheta, kamar yanda ya sabar mata kowacce ranan duniya. Yana shiga yasameta tana zaune afalo, yayinda gidan yayi shiru duk ana maida baccin da ba'ayiba Daren jiyan shiyasa ita da kanta ta shiga kitchin, hannunta riƙe da carbi tana ja,  rusunawa yayi agabanta cikin girmamawa yagaisheta cikin body language kamar yanda ya saba. Ko gama dai-daita zamansa baiyiba fitinannen ƙamshinta yayi masa sallama a hanci, lokaci guda kuma saigata tashigo cikin falon, sanye take da hijab wanda takawo har zuwa ƙasa, sosai hijab ɗin yayi mata kyau, cikin nutsuwa taƙaraso cikin falon Ummi naganinta tasaki murmushi tare da miƙo mata hannu, gefenta ta zauna, har ƙasa ta durƙusa cikin tsananin ladabi da girmamawa tace da Ummi "Ina kwana?." da "Lafiya Ummi ta amsa tare da tambayarta ya kwanan baƙunta? ɗan murmushin daya ƙara bayyana zallan kyawunta tayi cikin nutsuwa tace. "Alhamdulillah!." Da "Masha Allah!!." Ummin ta amsa, still fuskarta ɗauke da murmushi, hakanan taji wani irin daɗi ya ratsa zuciyarta don kwata-kwata bataiyi zaton haka yarinyar keda ladabi ba, shiru tayi tana kallon yatsun ƙafan Ummi haka nan taji son Ummi cikin ranta, cikin kula da sonta Ummi ta ɗan sunkuyo ta kalleta cikin sanyi tace. "Ngd ɗiya Allah ya muku al'barka ya bamu zaman lfya." cikin tsunkuyar ds kai da alamun jin kunya murya can ƙasa tace. "Amin Ummi." cikin kula Ummi tai murmushin jin daɗi tare da cewa. "Tashi kije ki kwanta kiyi bacci ki huta gajiyan biki." Cikin jin daɗi ta gyaɗa kai kana ta miƙe hankali tare da ficewa daga cikin falon, ko kallon inda Saifuddeen yake batayi ba, hasalima yi tayi kamar batasan da wani abu waishi mutum awajen ba, ita kuwa Ummi bataji wani abu akan rashin kula Saifuddeen ɗin da Zaleehan tayi ba, domin azotonta sunyi nasu gaisuwar a ɗaki, domin duk atunanin Ummin Saifuddeen ɗin aɗakin Zaleehan ya kwana. Zaleeha na tafiya Saifuddeen yaɗan zubawa Ummi shagwaɓansa sannan ya nufo part ɗin nasu. Koda ya shigo cikin falon zaune ya iske ƙanwarta Zaheera ta ƙurawa tv ido, inda take kallon wani series film a mbc bollywood wato (حب خادع) nasu tara da deep, kasancewar sosai dukansu ita da Zaleeha keson series film ɗin. Tana ganin Saifuddeen taɗan zamo daga kan kujeran gaishesa tayi, yayinda shi kuma ya amsa mata cikin jinjina mata kai, fuskarsa ɗauke da ɗan murmushi, kai tsaye ɗakin Zaleehan ya nufa, don rashin ganinta afalo da yayi ya tabbatar masa cewa tana cikin ɗakin, ahankali yakai hannunsa inda ya murɗa handle ɗin ƙofar, kana ya shiga, tsaye take agaban gado tana ƙoƙarin zuge zip ɗin rigarta dake a wawage, yayinda white skin ɗin bayanta keta shinning, jin motsin anshigo ɗakin yasanya batare da ta juya ba tace. "Zaheera zoki zuge min zip ɗin nan please." taƙare maganar tana me watsa dogon gashin kanta akan wuyanta. Ahankali ya danna madannin wheelchair ɗinsa, take keken tasoma tafiyu as slowly, yana ƙarasawa gab bayanta ya tsaya cak, hannunsa yakai kan lallausan skin ɗinta, jin sauƙan wani lallausan hannu abayanta wanda sam baiyi kama dana ƙanwarta Zaheera ba yasan yata juyowa da sauri. Idanunsune suka faɗa cikin na juna take kuma losing balance ya kamata nanfa ta faɗo kansa, hannayensa duka biyu yasa inda ya rungumota jikinsa, azabure cikin matsanancin tsoro ta turesa tare da tashi tsaye, cikin fushi tace. "Waya baka izinin shigomin ɗakina, har takai ka gayin azarɓaɓin taɓa mini jiki? ko an faɗa maka cewa na nemeka ne." tura baki tayi tare da dubansa cikin shakkarsa da takaicin aurensa da tayi tace. "Ni jikina na mutum ɗaya ne, kuma zan cigaba da adana masa kaina, sannan jikina bana musaki bane, jikina na cikakken namiji mai lafiya ne, halan ko kamanta cewa kai Nak...." Batare daya bari ta gama magananba ya wani irin fusgota ta faɗa jikinsa, hannunsa yasa inda yayi mata wani irin tsastsauran riƙo, cikin tsoro da fargabar zuciya ta ɗan kalato tsiwa tace. "Da Allah ni kasakeni, na tsani haɗa jiki da kai!." Ahankali yaɗan lumshe idanunsa wanda suka ɗan sanja launi, laɓɓan bakinsa yaɗan cije, "wato shi nakasashshe ne saboda haka bazai iyayi mata komai ba ko? hmmm zaiyi maganinta ne." yafaɗi maganar acikin zuciyarsa. hannunsa ɗaya yasanya ya tallafo fuskarta, ganin haka yasa Zaleeha waro idanunta, cikin mamaki ta ɓuɗe baki tare da da cewa. "Kai Malam da Allah miye haka zaka...." Kamar amafarki haka taji sauƙan bakinsa acikin nata, yayinda yasa hannunsa ya riƙe kanta da ƙarfi, tayanda bata iya ƙwacewa ba, idanu Saifuddeen ya lumshe tare da kamo sweet lips ɗinta yana tsotsa, cikin son ladabtar da ita ya shiga tsotsan bakinnata da ƙarfi ƙarfi, inda har teeth ɗinsa yake sanyawa akan lips ɗinta yana ɗan cizonsu, harshensa yasa ya naɗo nata harshen tare da kanainaye mata harshen take yashiga musanya yawunsu, firgici da takaici haɗi da tashin hankali Zaleeha kam tashigesu, sosai take son ƙwace kanta daga azabar tsotsar lips ɗinta dayakeyi amma takasa. Idanuntane suka ciko da ƙwalla, take tasoma dukan ƙirjinsa da duka ƙarfinta amma ina Saifuddeen ko gizau, saima ƙara zafafan tsotse laɓɓanta da yakeyi da ƙarfi. Azaba kuwa da zafi har cikin kanta, dan kansa ya janye bakinsa daga nata tare da hankaɗata kan gado, baya yayi da kekensa tare da dubanta giransa ɗaya ya ɗage mata tare dayi mata alaman to ya? Kuka mai cin rai tafashe dashi cikin matsanancin takaici haɗi da sabuwar tsanarsa tace. "Allah Ya isa na bazan taɓa yafe makaba mugun mugaye kawai, wanda babu abun daya sani sai son kai dana zuciya." hannu tasa tana goge harshenta data ɗan zaro kana idonta na zubda siraran hawaye tace. "Allah ya isana kuma Allah zai saka min" Murmushin daya bayyana tsantsar kyawunsa yayi ahankali ya ɗage kafaɗunsa alaman ko oho, madannin kekensa ya danna tare da juyawa ya fice daga cikin ɗakin, tana ganin fitarsa ta silalo daga kan gadon zama tayi aƙasa tare da sakin kuka, cikin matsanancin takaici tashiga harba ƙafafunta tamkar ƙaramar yarinya ƴar shekara 6, ji take kaman tayita zabga ihu na baƙin cikin abunda yayi mata, ga kuma bakinta dake masifar yi mata raɗaɗi harshenta kuwa har jinsa take kaman baya cikin bakinta, laɓɓɓanta sai wani zut-zut sukeyi, kuka takeyi tsakananinta da Allah tana harba ƙafafunta, cikin kukan tace. "Bazan taɓa yafe maka ba, mugu nakasashshe mai zubin ƴaƴan ruwa, wallahi ayau plant ɗina zai fara aiki bama sai gobe ba, don in na zauna da kai zalina zakayi taci." A garin Doho kuwa Mamace da yayarta Ruda ke zaune gaban wani shirgegen kasurgumin bokansu na arnan kan dutse bayan ya gama jin baya nansu sun gama tattaunawa, zuru-zuru yayi da ida nunshi tare washe wawakeken bakinshi cikin amo mara daɗin ji yace. "Kada ku damu, bazata zaunaba dan sihirin ya kamata, munyi sa'a lokacin da mukayi aikin bata salla, sihirin yana ƙarƙashin gadonta bazata iya zama cikin ɗakinba dole, zata gudu zata bar gidan babu zama da wannan gurgun, dan tuni mun gama aikinmu babu wanda zatayiwa biyayya akan zama a gidan, dan ji zatayi kamar cikin kushewarta take, mutanenmu zasu sa mata tsanan gidan da mijin sosai." cikin jin daɗi Ruda tace, "Yauwa boka bashallu mun gode." Mama kuwa kai ta jinjina tare da cewa. "To amman ya batun aurenta da Abdussalam?." kai ya jujjuya mata tare da zaro idonshi yace. "Ki bari kiga mun samu mun raba wannan aurenma tukun, dan shi yaron da wuya mu sameshi." jin haka Ruda tace. "Mun gode a gama wannan ɗin kafin a fara wani." itama Mama godiya tayi kana suka ajiye mishi kuɗin aikinshi suka tafi. ~Wasa farin girki~ By *GARKUWAN FULANI*[9/9, 9:05 PM] +234 806 222 4030: Cikin bedroom ɗin ta da nufin zataje ta sanarwa Ahmad, ko meye ta tuna kuma, oho sai ta koma ta zauna tana nazari. Sosai abun yayiwa Raliya ciwo, koda Ahmad ya fito ganin meya tsareta,  kamar zata faɗa masa saikuma tayi shiru, shi kuwa da bai san meke faruwaba sai janta yayi suka koma bedroom ɗinta dan yana tare da begenta. Ɓangaren Saifuddeen kuwa kwata-kwata ma bai nemi Zaleehan ba, yana fitowa daga wanka kwanciya kawai yayi,  sam bayaso yaje gareta, harma yaga abun da zai rabasa da nutsuwarsa, dan shikaɗai yasan irin azaban dayasha jiya, saboda haka baya sake fatan shan wani azaban kalan wannan, kasancewar agajiye yake hakan yasa yana kwanciya bacci ya ɗaukesa. Zaleeha kuwa gaba ɗaya tatakura akan kujeran da take kwance, sam kujeran bata da daɗin kwanciya bare daɗin bacci, cikin mintuna ƙalilan har jikinta yasomayi mata ciwo, gawani irin masifaffen sanyi dake busawa acikin garden ɗin, mutsutstsuka jikinta kawai takeyi, sosai takejin wuyanta ya ƙage amma kuma bata da wani zaɓi, wanda ya wuce yin haƙurin kwana awajen. Atakure haka bacci ɓarawo yasamu nasarar ɗaukarta. Ƙiran sallan asuban fari da akeyine ya ratsa jikinshi ya bashi lokacin salla yayi, ahankali ya buɗe idanunsa,  ɗan miƙa yayi tare da haɗawa da salati a zuciyarsa, nan yatashi zaune, kekensa ya jawo tare da hawa kanta, cikin nutsuwa da ɗan sauran kasalan bacci yakai kansa banɗaki, wanka yayi tare da ɗauro alwala, kaitsaye yafice daga ɓangaren nasa. Har yaƙarasa jikin ƙofar na Zaleehan saikuma wani tunani yazo masa, take yafasa shiga tada'ita da yayi niyya, sai ya ƙonƙasa mata ƙofar, kana ya juya ya tafi, kai tsaye yawuce masallaci. Zaleeha kuwa dama gaba ɗaya batayi wani ishashshen bacci ba, dan sanyine awajen sosai, jin motsi alaman cewa yatafi masallaci yasata tashi zaune, cikin sauri ta ɗau bargon haɗi da pillow'n ta, ahanzarce tanufi ƙofar falon nata, dai-dai lokacin Ahmad yafito daga ɓangarensu dan zuwa masallaci, idanunsa ne suka gane masa Zaleeha, fuskarsa ɗauke da ɗan mamaki yabita da kallo, ganin fitowarta daga cikin garden gashi hannunta riƙe da bargo da kuma pillow alamun nan ta kwana kenan yasanyashi girgiza kansa, cikin ransa yace. "Allah Ya shirya ki, ae dama mai hali baya taɓa fasa halinsa, saidai in ba'a zauna ba kuma dai duk tsaurin wayon amarya to wlh sai ansha manta anci sadaki an suɗe ki dai gama ɓoye-ɓoyenki." Nan yawuce masallaci. Itakuwa Zaleeha sam-sam ma bataga Ahmad ɗin ba, kaitsaye ɗakinta ta wuce, cikin hanzari tasoma rage kayan jikinta, ruwan ɗumi ta haɗa inda tayi wanka, tana fitowa daga wankan ta zura wata farar jallabiya mai kyau,  hijab tasanya tare da ta da sallah, koda ta idar da sallan bata tashi akan sallayan ba saida tayi azkar, nan ta ɗauko ɗan ƙaramin Qur'aninta tasoma karatu,  ba'ita ta rufe Qur'anin ba saida taga gari yaɗan somayin haske, wasu bedroom slippers masu kyau ta zura aƙafafunta, inda tasake feshe jikinta da turare me daɗin ƙamshi. Koda tafito daga ɓangaren nasu kai tsaye part ɗin Ummi ta  nufa, bakinta ɗauke da sallama haka ta kutsa cikin falon, wanda ke cike da jama'a, Raihana ne da Saminu waƴanda zasu koma Kaduna asafiyar ta yau, saikuma Goggo Dada da Aunty Meena wanda zasu koma Dukku, Aunty Rahama ma yau zata koma, don tunjiya Dr.Adnan keyi mata waya, kan cewar yayi kewarta gashi weekend  yana gida shiyasa yace zaizo da safen ya ɗauketa. Cikin yin ƙasa da kai haɗi da nuna tsantsar ladabi taƙaraso cikin falon,  har ƙasa ta durƙusa inda ta gaishe da Ummi, cikin fara'a haɗi da sakin fuska Ummi ta amsa mata gaisuwan nata, tare da miƙo mata hannu ta kamo nata, cikin kulawa Ummi tace. "Taso kizonan kusa da Umminki yarinyar kirki, kema ai ɗiyatace, tunda kika shigo cikin mu kuwa kinzama jininmu." Tasowa tayi daga inda take tare da ƙarasowa kusa da Ummi, Ummi ne tajawota inda ta zaunar da ita agefenta, sadda kai ƙasa Zaleeha tayi tana murmushi, hakanan itakam Allah ya samata son matan aranta, sosai take ganin ƙima da kuma darajan Ummi'n,  su Raihana ne suka gaishe da Zaleehan, amatsayinsu na ƙannen Saifuddeen,  haka ta amsa musu fuska asake, ɗan zamowa ƙasa tayi inda tagaishe da Goggo Dada dakuma Aunty Meena, sai kuma babbar yaya wato Adda Rahama, da kuma Saminu wanda ke zaune gefen Saifuddeen, da fara'a akan fuskarsu duka suka amsa gaisuwar nata,  komawa gefen Ummi tayi ta zauna a ƙasan carpet dan tana matuƙar ji da ganin darajar Ummi, shiru tayi yayinda ko kallon inda Saifuddeen yake batayi ba, shikuwa har acikin ransa mamakin irin tsantsar ladabinta ga ƴan uwansa yake, tanason kowa acikin ahalinsa tana mutuntasu da girmamasu, amma wato shine marainin wayonta sam bata ganinsa da gashin ido, murmushi yayi wanda  shi kaɗaine yasan ma'anonin murmushin ransa yace.   tabbas kuwa zanyi maganinta ne, very soon zankashe bakin tsiwan, badai ni ta raina ba?." hmmm yasha alwashin duk randa ya kamata kuwa zataji ajikinta. Saminu ne yace da Raihana su hanzarta sutafi, bayason tafiyar da bata safiya ba, saboda alokacinne yakejin karsashi ajikinsa, nan kowa yatashi don yi musu rakiya zuwa compound ɗin gidan, ciki kuwa harda Zaleeha wanda ta kamo hannun Daddy yaron Bappa Ali wato Junior mai sunan Abbandu Saifuddeen kenan,  kasancewar yaron kyakkyawane yasanya sosai yashiga ranta, gashi nan da wayonsa irin yaran nanne masu shiga zuciya, haka suka fito compound ɗin gidan inda yaketa zuba mata surutu, itakuwa murmushi kawai take tayi masa, har bakin mota suka rako su Raihanan, nan sukayi sallama da juna, cikin yanayi na tsokana Raihana ta dubeta, tare da cewa. "Kikulamin da Hammana da kyau da kyau, dan ko ƙuda bama son ya taɓa manashi." Dariya sukayi gaba ɗayansu, itakuwa Zaleeha ɗan guntun murmushi tayi, yayinda taji wani malolon abu ya tokare maƙoshinta, cikin zuciyarta tace. "Lallai kuwa zai mutu, indai nice zan kula dashi!. Yo ni me haɗina dashi kunamai ma su sauƙa ajikinsa mana ba ƙuda ba ni me yadameni." Motar su Raihana baigama fita daga gidan ba saiga Dr.Adnan nan shima yazo ɗaukar matarsa, nanfa suka gaisa, inda Zaleeha tagaishesa cikin mutuntawa,  Farouq da Adam kuwa sai tsalle suke dan sunga babansu, duk girmansu baigani ba haka yasasu ajikinsa,  babu yanda basuyi ba akan cewa Daddy yazo su tafi ba amma yaƙi,  waishi ala dole yasamu sabuwar Aunty yace shi Dukkunma bazai komaba, kusan saida yabawa kowa dariya haka suka tafi anata raha. Daddy kuwa da ƙyar  suka iyayi masa wayo yabi iyayen nasa da karatunshi,  Ahmad ne yazo da motarsa wanda dama shine zai mayar dasu Goggo Dada gida, lokaci ɗaya fa gaba ɗaya jama'an baƙin biki  suka watse gida yayi shiru. Ummi Raliya da kuma Zaleehan kawai aka bari, dama Saifuddeen yana part ɗin Ummi, kasancewar shi baifito rakiyan ba, shikuwa Hayatudden sarkin bacci, yanacan tun dawowansa daga sallan asuba daya koma bacci shine haryanzun baitashi ba. Direct Zaleeha part ɗinta ta koma, inda su Ummi da Raliya suka koma wajen Saifuddeen. Tana shiga cikin ɗakin nata ta cire hijabin dake jikinta, kan gado ta faɗa tare da ɗan lumshe idanunta, sosai takejin wani sabon bacci naƙoƙarin ɗaukarta. Can ɓangaren Ummi kuwa, Saifuddeen naganin dawowansu, ya sakawa Ummin nasa shagwaɓa, sanin halinsa na sakalci kaman wani ƙaramin yaro yasanya Ummi da kanta tashiga kitchine inda ta haɗa masa coffee, sosai yaji daɗin haɗin coffee ɗin da Ummin tayi masa, ɗaukan mug ɗin yayi tare da bar musu falon, kai tsaye yanufi sashinsu. Saifuddeen nafita, Ummi tayi murmushi cikin jin daɗi tace. "Allah kenan maiyin yadda yaso a lokacin da yaso, kafun auren nan kowa yasan cewa yarinyar nan bason auren nan take ba, amma yanzu cikin ƙuduran Allah gashi suna zaune lafiya, kinga ta saki ranta." Murmushin gefen baki Raliya tayi tare daɗan muskutowa, cikin jimamin abun dake damun zuciyarta tun daren jiya tace. "Hmmmm hakane kam Ummi, amma nikuwa jiya naga abun daya ɗauremin kai ya bani mmki, dan nima da fari da naga ta saki ranta naji daɗi." Dubanta Ummi tayi tare da cewa. "Mene kuma yafaru?." Gyara zama Raliya tayi tare da cewa. "Ummi kinsan kuwa cewa jiya awaje cikin garden ta kwana? wallahi Ummi abun yabani mamaki sosai, inata tunanin dalilin da zaisa ta kwana cikin garden, idan har zatana gudunsa haka, meyasa ta amince da aurensa?." Cikin matsananci mamakin jin maganan da Raliyan ta faɗa Ummi ta sauƙe wani irin ajiyar zuciya, jiki amace tace. "Raliya kin tabbatar da abun da kike faɗa kuwa?." Kai Raliya tajinjina tare da cewa. "Wallahi Ummi da idanuna naganta jiya a garden ta kwana, kuma koda natashi sallan asuba dana leƙa naganta, alokacin tana ƙoƙarin barin wajen, kuma tabbas nasan babu makawa itace dan Abban Farida ma ya ganta dayazo tafiya masallaci." Ɗan jim Ummi tayi tare dajinjina kanta, take taji zuciyarta tayi mata wani irin ba daɗi, hankali ya tashi fargaba ya cika mata zuciya wato har ƙiyayyar ta kai haka, jiki a mace tace. "To Allah dai ya kyauta." Amin Amin Raliya ta amsa jiki a mace. Haka dai zaman yaci gaba da gudana har tsawon kwanaki, Kullum  in gari ya waye Zaleeha na idar da salla zataje ta gaida Ummi a mutunce, lokuta da dam takan samu Saifuddeen a wurin Ummi, amman tsakaninta dashi sai harara da murguɗa baki, tana son kowa na gidan yayinda suma duk suke matuƙar sonta musamman Raliya da takanje har ɗakin Zaleeha su ɗanyi hira, dan itacema ta tayata shirya tarin akwatunan kayan aurenta da kimtsa mata duk abinda zata buƙata a durowa, sauran akwatunan suka kaisu ɗaya ɗakin, Hayatuddeen kuwa dama akwai sabo a tsakaninta haushinta da yaji kan cewa da tayi bata son Hammanshi yanzu babushi tunda yanaga har ta yarda da auren ta zauna lafiya dashi. tana matuƙar girmama Ummi wanda hakan yasama mata soyayya a idanunsu, tana mutunta Ahmad a cewanta mai sunan yayanta ne dan Yaya ma take kiranshi tun tana gaidashi yana amsawa a yatsine har dai ya fara ɗan sasaautawa. Har yau kuma a woje take kwana cikin gardin, wannan abun shine yasa Ahmad yake matuƙar jin baƙin cikinta, shi kuwa Saifuddeen  da fari baisan bata kwana a ɗakintaba dan baya shiga kuma da safe yana ganinta a wurin Umminshi, To tun shekaran jiya daya dare ya ankara da bata ɗakin, ya dudduba ko ina na cikin part ɗin nata babu ita ba dalilinta, falonshi ya koma wayarshi ya ɗauka tare da yin mgnar zuciya, "To ina take zuwa ta kwana yau kwana biyu kenan bata kwana a nan." Kanshi ya ɗan jingina da jikin kujerarsa tare daci gaba da mgnar zuci. "To waya sanima ko ta daɗe da barin kwana a nan." sai kuma yayi ajiyan zuciya tare da cewa. "ko dai part ɗin Ummi take kwana? kai Anya kuwa Ummi zata barta ta kwana a side ɗinta, to ko dai part ɗin Raliya take kwana." Text ya rubutawa Ahmad, "Kayi bacci ne?." Ahmad da ke zaune a falo shida Raliyya suna mgnar Zaleeha dan hango wucewarta da sukayi, murya a sanyaye Raliya tace. "To wai ko dai Hamma Saifuddeen bai san bata kwana a ɗakinba?." Ajiyan zuciya Ahmad ya sauƙe tare da cewa, "Ina zaton bai saniba, kinfa san shi da miskilanci, in kuwa yasan bata kwana a cikin to yasan inda take kwanan shiyasa bai kulataba ai jiki magayi." da sauri ya ɗago wayarshi ganin saƙon Saifuddeen ne ya sashi cewa. "To ina ga dai bai san bata kwana cikiba sai yanzu dan ga text ɗinshi wai nayi bacci ne." ido Raliya ta zuba fuskar wayarshi tana ganin amsar da yake rubuta mishi. "A a banyi bacci ba, lfy dai ko?." jim kaɗan sai ga wani saƙon. "To lafiya dai zance,amman Zaleeha na wurinku ne?." murmushi Ahmad yayi tare da cewa Raliya, "Hmmm zanyi mgnin yarinyar nan." sai kuma ya rubuta mishi amsa. "A a Zaleeha kuwa, bata nan." a take sai ga wani saƙon. "Kasa Raliya ta dudduba nan wurinku, taje Side ɗin Ummi ma ta duba ko tana can." yana gama karan tawa yace. "Lafiya dai kam ko?." tsaki Saifuddeen ya ɗan ja kana ya rubuta mishi, "Nima ban saniba lafiya ko ba lfy ba, ina dai zargin yarinyar bata kwana a gidan nan, dan tun shekaran jiya na lura babu motsinta, sannan yanzu na dudduba ko ina bata ciki side ɗin." cikin nuna fargaba Ahmad yace. "Innalillahi, to ina take zuwa ta kwana, gani nan fitowa." sai ya kuma miƙe ya kalli Raliya tare da cewa, "Maza kije side ɗin Ummi ki gaya mata, ana neman Zaleeha ki kuma ce karta nuna tasan inda take kwana zanyi mgninta." to tace tare da juyawa ta nufi side ɗin Ummi, kana shi kuma Ahmad ya nufi ƙofar falon Zaleehan nan yayi kicibis da Saifuddeen daya fito, "To wai ina ta shigane, mufa mun dudduba wurinmu babu ita." kai ya jujjuya mishi alamun shimafa ya dudduba wurinsu babu ita. dai-dai lokacin kuma Ummi da Raliya suka iso, nan fa suka haɗu suka nuna basu san inda takeba. ita kuwa Zaleeha tun fitowan su Ahmad ta buɗe ido, jin ita ake nema yasa ta zame a hankali ta konta a ƙasan kujerar fulawi ke zagaye da ita. Ahmad kuwa yana hangota hakan ya sashi cewa. "Hmmmm zaki gane kurenki." wayarshi ya zaro lallatsata yayi ya nemo number Ya Aminu, ya kirashi kana ya kara wayar a kunnenshi. Can cikin bacci Ya Ameenu yaji wayarshi nata suwa, a hankali ya ɗan zare Maryam daga jikinshi, hannu yasa ya ɗauki wayar time ya duba ƙarfe ɗaya na dare. "Ahmad kuma a daren nan lfy kuwa?." sosai yaji fargaba ,kar dai Zaleeha nacan na tarfa musu rashin ɗa'a, jiki na rawa ya amsa kiran cikin sauri yace. "Salamu alaikum ,Ahmad lfy kuwa?." cikin nuna tashin hankali yace. "Ya Ameenu Zaleeha ce bamu ganiba mun nemata ko ina a gidan babu ita ba dalilinta, kuma Saifuddeen yace tun shekaran jiya bata kwana a side ɗinsu, to sai yayi tunanin wai ko side ɗinmu take shigowa ta ɓuya ko na Ummi, to shine yanzu ya sanarmana zatonsho tana wurinmu,mun duba kab gidan bata, nan shine nace bari in kiraka ko ta dawo gidane?." cikin kaɗuwa Ya Ameenu ya miƙe tare da cewa. "Zaleehan to ina take zuwa?." a taƙaice Ahmad yace. "To ko tana gida ne?." rai a ɓace Ameenu yace. "Kai anya kuwa sam bata gida, to ina take zuwa ta kwana, yi haƙuri bari in kira Baba malam." to Ahmad yace kana ya katse kiran sannan ya gaya.musu yadda sukayi da Yayanta Ameenu, kana yace su shiga ciki kafin Ameenun ya kirashi. Shi kuwa Ya Ameenu wani irin tashin hankali ne da ɓacin raine mai tsanani ya rufeshi to ina Zaleeha take zuwa ta kwana ina take tafiya ta bar ɗakin mijinta me haka yake nufi? kiran Baba Malam yayi bawan Allah yana zaune bisa sallaya yana karatun qur'an kiran Ameenu ya shigo wayarshi, har wayar ta katse bai ɗaukaba duk da yaga Aminune so yake yaje ƙarshen surar Arrahaman da yake karantawa, yayinda wani fargaba ya rufeshi lfy kuwa kira da tsakiyar daren nan. Yana zuwa ƙarshen surar kira na uku na shiga wayar, da hamzari ya amsa kiran, "Barka da dare Baba Malam kayi haƙuri na tada kai daga bacci." Ameenu ya faɗa a ladabce, murya a ɗan harɗe Baba Malam yace. "Ameenu lfy kuwa meke faruwa?." cikin sanyi Ya Ameenu yayi mishi bayanin da Ahmaɗ yayi mishi, ya ƙara da cewa. "Ko dai ta taho gida ne?." lumshe ido Baba Malam yayi yana jin wani irin suya da zuciyarshi keyi me Zaleeha ke nufi zubda mishi mutunci da kima  a idanun mutane ko? a hankali ya cewa Ameenu. "Ameenu bana zaton tana cikin gidana ,bazata zo nanba, amman dai bari in bincika." to Aminun yace kana y katse kiran. shi kuwa Baba Malam fitowa yayi da kanshi yayi tabin luggu da saƙo na gidan ya duba ko ina kab babu ita, koda ya titse Mama da tambayar ina Zaleeha ke zuwa ta kwana, rantse-rantse tayi ta mishi akan ita bata san ina Zaleeha ke zuwa ta kwanaba. a daren Ameenu ya kira goggonsu Maryama da duk inda suke zaton zataje ko ina sai ace musu bata zoba. Wannan abu yayi matuƙar tada hankalin Baba Malam ya Ameenu kuwa ji yake in yaga Zaleeha zai kusan karta, dole ya kira Ahmad yace, wlh bata wurinsu amman tunda da safe tana dawowa zai zo ya sameta, har ɗakinta. Da  wannan kowa ya koma ɗakinshi, Ahmad kuwa ranshi ƙal yasan Zaleeha zata gane kurenta. Washe gari kamar yadda ta saba, suna tafiya masallaci ta koma ɗakinta wonka tayi da ruwan ɗumi wai ko tsamin cizon sauro da  jikinta keyi zai ragu, wanka da al'wala tayi, kana ta fito tazo tayi salla koda ta idar  azkar tayi sanan ta miƙe ta kimtsa jikinta cikin wata doguwar rigar mai ɗan karen.kyau wanda duk na kayan aurene, da mayafinshi ta yane kanta ,kana ta nufi sashin Ummi. a falo ta samesu, dukansu, cikin nitsuwa ta isa gaban Ummi dake mata murmushi tare da cewa. "Gari ya waye ko ɗiyata?." murmushi tayi tare da rusunawa gaban Ummi cikin ladabi da sanyin lafazi tace. "Ummi Ina kwana?." cikin kula Ummi tace. "Lafiya lau ya  baƙunta?." kai a sunkuye tace, "Alhamdulillahi." "Masha Allah." cewar Ummi kenan Hayatuddeen ne ya gaidata ta amsa fuska a sake, kana ta kalli, Ahmad dake zaune kusa da Saifuddeen bisa alamu lissafi sukeyi, cikin sanyin sauti tace. "Yaya ina kwana?." a taƙaice yace. "Lafiya lau." daga nan kuma sai ta miƙe tare da cewa Ummi . "Raliya na kitchen  ko?." cikin jin daɗi Ummi tace. "A a tana sashinta yau wai kanta ke ciwo." a hankali tace, "Ayyah ban saniba Allah ya bata lfy." Amin Amin Ummi tace, Kana sai ta ɗan rusuno tare da cewa, "To Ummi bari in shiga kitchen, me zan  haɗa  mana breakfast?." sosai Ummi take jin daɗin yadda take sakewa da Raliya su shiga kitchen tare, gashi yanzu har tana shiga ita ɗaya ma tayi musu girki. cikin kula Ummi tace. "Bari inzo mushiga tare to." da sauri tace . "A a Ummi ki bari zan iya ki huta." sai kuma ta kalli Hayatuddeen daketa murmushi tace, "Zo muje kitchen ka tayani hira." da sauri ya miƙe yabi bayanta, yana cewa. "Yauwa muje ki min dege-dege." da ido Ummi ta bisu har suka shiga kitchen ɗin. koda suka ƙarasa cikin kitchine ɗin, hayewa kan wata kujera Hayatuddeen yayi ya zauna, wayarsa ya fiddo daga aljihunsa tare da soma latsawa, ita kuwa Zaleeha, direct wajen fridge ta nufa, buɗe cikin firjin dake shaƙe da kayayyakin abinci tayi, nan ta zaɓo manya manyan kaji guda biyu,  sake wankesu tayi sannan ta ɗaura akan wuta tare dasa kayayyakin ƙamshi dana danɗano. nan ta ɗibo irish patatoe tasoma ƙoƙarin ferewa,  Hayatuddeen ne ya taso tare da soma taya ta,  haka suka cigaba da firan, yana ta zuba mata surutu,    mayafin dake jikinta ta ajiye, tare da soma yin aikinta cikin nutsuwa, yayinda Hayatuddeen gaba ɗaya ya sakota gaba da surutunsa,  cikin abun da bai wuce awa ɗaya da rabi ba, ta kammala haɗa barbecued chicken da kuma patotoe balls,  sai kuma bread Pizza, wanda gaba ɗaya ƙamshinsa ya cika kitchine ɗin, Hayatuddeen dake zaune agefe sai haɗiye miyau yake, dan har ya tsara irin cin da zaiyiwa bread pizza ɗin, da ƙamshinsa ya cika masa hanci, spearmint tea ta haɗa, sannan ta juyesa acikin flask, nan ta kimtsa gaba ɗaya kayan akan wani babban tray, duban Hayatuddeen tayi tare dayi masa alama akan yazo ya tayata ɗauka, aikuwa shi ya kwashe komai inda ya jere musu break fast ɗin akan dinning table, ita kuwa Zaleeha har yanzu tana kitchine, fruit salad ta haɗa, inda ta zubashi cikin wani babban glass bowl, tunanin haɗa chocolate fudge cake ne yazo mata, nan ta duba taga akwai komai na buƙata, kanta ta jinjina, sannan tashiga ƙoƙarin haɗawa, cikin mintuna ƙalilan kuwa ta kammala, ita kanta saida tayaba da ƙamshin chocolate fudge cake ɗin, Hayatuddeen dake falo kuwa koda ƙamshin yaje masa, saida yakasa haƙuri ya biyota zuwa kitchine ɗin, ganin, fudge cake ɗin yasan yashi cewa. "Wow fantastic, Aunty Zalee dama wai kin iga girki har haka ne?, na ɗauka a faɗa da masifa chart da zuwa wurin aiki kawai kika iya." Hannu tasa takai masa bugu, da sauri ya kauce yanayi mata dariya, hararan wasa ta watsa mai, tare da cewa. "Kaɗauka yanda kuke sakarkaru kaida Zakariyya haka kowa ma yake ne baku da aikin sai yawo a gari dama tsokana da ci." Taƙare maganar tana me miƙo masa, wani haɗaɗɗen tray wanda ciki tashirya chocolate fudge cake ɗin, amsa yayi yana wani malau malau da baki, tare da cewa. "Hmmm ai yanzune ma zakuga tashen jami'a zakusha mmki bari dai in gama sabawa da jami'ar kin san banfi sati ɗaya da fara zuwa ba." Dariya ta ɗanyi tare da cewa. "Yo ai da an ganka ansan kanka na fizga da igiyar iskar sabin shiga jami'a ka dai yi a hankali yaro dan ita jami'a gidan ban kashine." Murmushi ya ɗanyi tare da cewa. "Gobe zan kawo miki sabon abo kina Khamis ku gaisa. kiga irin salon takun mu, yaseen ki kuma cewa mijinki ya saya min mota. Dan ni ba yaro bane da za'a rinƙa kaini ana ɗaukoni kamar wani ɗan primary ko kayan wonki da za'a rinƙa kaini ana ɗaukoni". Ya ƙarishe mgnar yana wuce zuwa dinning, food flask ɗin dake gefenta wanda ciki ta shiryawa Raliya abinci ta ɗauka. Koda ta fito falo, nan ta iske Ummi, da kuma Saifuddeen, da Ahmad, Hayatuddeen kuwa tuni ya baje kan dinning, inda ya turo baki gaba, wai don saboda yace suzo suci, sunce yajira Zaleehan tagama sai suci tare, sam shi gaba ɗaya yaƙosa yaji yana tauna abincin, musamman ma da ƙamshin abincin ya cika masa hanci. Zaleeha na fitowa daga kitchine ɗin ta dubi Hayatuddeen, fuskarta ɗauke da murmushi tace. "Autan Ummi sarkin ci!." Baki Hayatuddeen yaƙara turowa gaba, ashagwaɓe yace. "Eh naji, amma please kice musu suzo muci, I swear am feeling hungry fa!." yafaɗi maganar yana me shafa cikinsa, wanda hadda ganin abincin ma yaƙara masa jin yunwa. Murmushin daya bayyana zallan cute face ɗinta tayi, tare da girgiza kanta. Ummi ne tayi murmushi tare da duban Zaleehan, cikin so da ƙaunar yarinyar tace. "Sannu da aiki, Allah yasaka miki da al'khairi, ya kuma baki ƴaƴa masu al'barka, wanda zasuyi miki fiye da haka." Saɗa kai kasa Zaleeha tayi tare da ɗan sakin guntun murmushi a kunyace murya a sanyayaye tace, "Amin Ummi." Saifuddeen kuwa a fakaice ya ƙura mata idanu, yana kallon duk wani motsinta sosai yake mamakinta, har yau har yanzu ya rasa ita wace irin mutum ce mai fuska biyu da jujjuyawa tamkar hawainiya, ji yanda take ta murmushi tare da sakewa dasu, tanayin komai kamar wata wanda keson zama dasu da gaske. Shi mamakinta ma yake, tawani irin sakewa sai kace ba itace, su keta gantalin nema ba jiya. Kawar da kansa yayi daga kallonta, tare da maida hankalinsa, ga laptop ɗinsa, wanda a zahiri laptop yake kallo a baɗiri kuwa fuskata yake kallo ta cikin madubin system ɗin, rumtse ida nunshi yayi a hankali tare da sauƙe nannauyan ajiyan zuciya, "To ina take zuwa ta kwana dasu waye take kwana, me take aikatawa a inda take kwanan?." haka yaji waɗannan tambayoyin sun cika mishi zuciyarshi dake cike da azabebben kishi, gaba ɗaya ya rasa wani irin kishi Allah ya ɗora mishi a kanta ji yake tamkar zai faɗi ya mutu dan baƙin ciki. Ahmad kuwa dubanta yayi tare da sakin murmushi, cikin ransa yayi ƙwafa, ahankali yace. "Zaki sanine yarinya." Duban Ummi Zaleeha tayi tare da ɗan rusunawa, cikin nutsuwa tace. "Ummi bari na kaiwa Raliya abincinta, tunda batajin daɗi nasan ba lallaine tasamu fitowa ba." Sosai Ummi taji daɗin kulawan da Zaleehan ta nuna ga Raliya'n, amma sai tace. "A'a Zaleeha da kanki, bazaki bari Hayatuddeen yakai mata ba." Murmushi Zaleeha tayi tare da cewa. "Bakomai Ummi, kinga Hayatudeen ɗin yace bazai iya komaiba sai yaci abinci,inaga bazai iya matsawa akan dinning ɗinnan batare daya lodawa cikinsa abinci ba, kin sanshi acicine kazar birni!." Zaleehan tafaɗa tana kallon Hayatuddeen, ba iya Ummi ba harta Ahmad saida yaɗanyi murmushi sabida sunan data kira Hayatuddeen Acici kazar birni, Ummi ce tace, idan takaiwa Raliyan abincin ta dawo suci abincin, nan tace zasuci da Raliyan acan. Koda ta ƙarasa ɓangaren Raliyan, akwance ta isketa, nan ta shiga ɗan kimtsa mata ɗakin, daga nan kuma ta zuba musu abincin inda suke ta hira ita da Raliya'n sosai Raliyan ta sake da ita har taji ciwon kan nata ya saketa. A falon Ummi kuwa, tuni Ummi tayi serving ɗin kowa, nan fa Hayatuddeen yasoma kai loma, yana me jijjiga kansa. Saifuddeen kuwa ahankali yake tsakuran abincin yana kaiwa bakinsa, idanunsa kawai yake lumshewa sabida ƙuna da zuciyarshi keyi na kishi, tabbas ya yaba da iya girkinta domin sosai abincin yayi masa daɗi, sam koda wasa bai taɓa tunanin cewa Zaleeha ta iya girki har haka ba. Ummi ma sosai ta yaba da abincin, Hayatuddeen kuwa cikin santi ya ɗago kai inda ya dubi Ahmad, cikin halinsa na tsokana yace. "Wallahi Aunty Zalee ta iya abinci, mai daɗi kaman kunnena zai fita, hmmmm ai daga yau ita zatana mana girki, don sosai tafi su wance iyawa." Dariya ne ya ƙwacewa Ummi, dan tasan tabbas Hayatuddeen dan tsokana yayi maganan da Raliya yake. Harara Ahmad ya watsa masa tare da taɓe baki, cikin nuna cewa shima matarsa gwanace yace. "Oho dai, da makaho ya rasa ido sai yace da wari, wannan har wani abinci ne, an haɗamu da tarkace saikace wasu yaran larabawa, jifa wani cake na chocolate, ko ance mu yaran larabawa ne, ai dai Raliya tafita iya girki ko Ummi." Ahmad ya faɗa yana me duban Ummi. Murmushi Ummi tayi tare da gimtse dariyarta, ita dai bata da tacewa, to ma mezatace komai tace yanzu zasuce tayi sonkai. Hayatuddeen kuwa dariya yadinga yi, don yasan maganan Ahmad ɗin, a iya laɓɓan baki kawai take, ba taje zuci ba, ya faɗane kawai don ya kare matarsa, amma yasan cewa koma waye yaci girkin dole ya yaba, musamman ma spearmint tea ɗin dake ta ƙamshin kayan haɗi, uwa uba kanasha kanajin wani irin ɗan ɗanon zuma aciki. Ahaka suka kammala cin abincin, inda Ummi tasa Hayatuddeen ya kwashe kwanukan yakai kitchine. Acan gidan Baba Malam kuwa, tuni Baba Malam ya ƙira Habu, inda yace yaje gidan Zaleeha ya taho masa ita. Babu ɓata lokaci kuwa, Ya Habu yashiga cikin motarsa, kai tsaye ya nufi gidan su Saifuddeen. Aƙofar gidan yayi parking motarsa, inda yayi knocking gate ɗin gidan, maigadi ne ya leƙo tare da buɗe masa, duban maigadin Ya Habu yayi tare da basa hannu suka gaisa, dai-dai lokacin kuma Ahmad yafito daga part ɗin Ummi zaiyi nasu sashin, ganin Ya Habu yasanyashi ƙarasowa wajen daɗan sauri, nan yabawa Ya Habu hannu sukayi musabaha koda Habun ya gaya mishi saƙon Baba Malam, Ahmad ɗinne yayi masa jagora har zuwa part ɗin Ummi, amutunce suka gaisa da Ummi, bayan sun gama gaisawanne yayi musu bayanin cewa Baba Malam ne yaturosa akan cewa ya tafi da Zaleeha, aikuwa sosai zuciyar Ahmad tayi fess, Ummi ne tace da Hayatuddeen yaje yaƙirawo Zaleehan, don kuwa har yanzu tana nan a part ɗin Raliya. Koda Hayatuddeen yaje part ɗin Raliya, nan ya iskesu sunata hira, shaida mata ƙiranta da akeyi yayi, "Aunty Zaleeha Ya Habu yazo yana falon Ummi yace kije." Cikin tsoro da fargaba tace. "Ya Habu kuma! Shi da waye?." murmushi Hayatuddeen yayi tare da cewa. "Ya Habu fa nace ba dodoba, shi kaɗai mana yazo, kinga yace kiyi sauri gida zakuje tare." Ƙulullluuuu cikin Zaleeha ya bada sautin murɗa a take cikinta ya ɗuri ruwa, nan ta cika da fargaba haɗi tsoro, cikin tankwashe wuya ta kalli Hayatuddeen tare da cewa. "Pleees je kace baka ganni ba." Sosai suka cika da mamaki, Kai Raliya ta sunkuyar dan kar dariyan da ke sun kubce mata ya baiyana a fuskarta, cikin mmki tace. "Ya kuma zaije yace bakyanan bayan kuma gaki?." kwaɓe fuska tayi tare da cewa. "Eh yaje yace ina bacci to." sosai tsoronta ya baiyana a fuskarta ganin hakan yasa yakoma falon Ummi yafaɗi cewa. "Bai ganta ba." Hararan da Ahmad ya watsa masa ne, yasan yashi faɗin gaskiya inda yace. "Tace nace banganta ba, ko kuma ince tayi bacci." Nanfa Ya Habu yacika da mamaki, take kuma yaji ransa ya ɓaci, ta tabbata mara gaskiya kenan, sake tura Hayatuddeen ɗin yayi akan tazo, nan ma Hayatuddeen yaƙara dawowa, yace tace wai batanan, haka akayi juyin duniya akan Zaleeha tazo, amma ina sam taƙi zuwa, daga ƙarshema ɗakin Raliya ta gudu ta ɓuya. Rai aɓace Ya Habu yafito yabar gidan. Yana zuwa gida ya iske Ya Ameenu da Baba Malam azaune, cikin ƙunan zuciya ya kwashe duk abun da ya faru ya faɗawa Baba Malam, sosai Ya Aminu ya hatsalo gaba ɗaya jikinshi rawa ya ɗauki saboda matsanancin ɓacin rai da zafin zuciya irin nasu na sojoji da kuma fulani ji yake muddin gata gashi zai kakkarya mata ƙafafuwa yaga gobe da wanne sawun zataje yawon. Me Zaleeha takeson maidasu ne?, me take nufi dasu? Wai ko dai gani take tafi ƙarfinsu ne? miƙewa yayi tare da cewa. "Bari inje in taho da ita!." Kai Baba Malam ya gyaɗa mishi dan fitinar Zaleeha tana tafasa mishi zuciya tana gab da ƙureshi. Ahmad na zaune afalo suna mamakin halin na Zaleeha, saiga ƙiran wayar Ya Aminu yashigo wayarsa, ɗauka yayi ko gaisawa Ya Ameenu bai bari sunyi ba, yace da Ahmad ɗin yana ƙofar gida, cikin jin daɗi Ahmad ɗin yasanar dasu Ummi da Saifuddeen. Sannan yafita ya shigo da Ya Ameenu'n, gaisawa sukayi sannan Ahmad ɗin ya dubi Saifuddeen, cikin nutsuwa yayi wa Saifuddeen ɗin alama kan cewar yayi haƙuri, zasu tafi da Zaleehan, Baba Malam ne ke nemanta, cikin body language Saifuddeen yace. "Bakomai" dan shi kanshi yana cike da son sanin ina take zuwa ta kwana. Shikuwa Ya Ameenu kai tsaye cewa kawai yayi anuna masa ɗakin da Zaleehan take, a bashi izinin shiga zata fito, nan Ahmad mugu yace. "Ba komai ya Ameena ai kai ba baƙo bane, tana ɗakin Raliya muje in nuna maka ɗakin". cikin zafin jini Ya Ameenu yabi bayan Ahmad da yake ta dariyar zuci so yake adaka mishi hegiyar yarinyar nan mai ladabin kura Zaleeha na rakuɓe ajikin bango suna magana da Raliya sai gani tayi an turo ƙofar ɗakin, koda takai dubanta ga ƙofar kuwa saida numfashinta yakusan ɗaukewa ganin Ya Ameenu a bayan Ahmad sam bata tsammaci ganinsa ba, aruɗe tasoma ƙoƙarin guduwa, taku ɗaya yayi ya cafkota tare da wanka mata wani irin gigitaccen mari, wanda yasanya tasaki wata irin razanannen ƙara, take tasoma ƙoƙarin shiɗewa, aharzuƙe Ya Ameenu yace. "Wato har kinyi girman da Baba Malam zai aiko ƙiranki kiƙi zuwa ko?, wuce muje kona kakkaryaki anan wajen, mahaukaciya kawai muje yau sai kin gaya mana gidan ubanwa kike zuwa ki kwana?!!." Cikin ɗimaucewa Zaleeha ta wuce gaba, tare da fara tsalle tana yarfa hannu cikin kukan gano yau sai dai buzunta dan ta lura zargin yawo Ya Aminu da sauran ƴan uwanta suke mata. jin ya sake yarfa mata wasu tagwayen marukane tare da ce mata. "Gidan ubanwa kike zuwa ki kwana? Wato mu zaki maida sakarkaruko? Wato yawon lalata kikeson ki koyaka?." wani irin tsalle ta rinƙayi tana yarfa hannu cikin tsananin kuka da tsoro tace. "Wallahi Ya Ameenu ba yawon lalata nakeyiba, a cikin gidannan nake kwana cikin garden nake kwana wlh bana fita ko ƙofar gidan." Ummi kam dake falonta jin kukan Zaleeha ne yasata saurin juyowa ta kalli Saifuddeen dake kallonta tace. "Kai Saifuddeen dukanta fa sukeyi ,kada ka bari su tafi da ita zasu illatata,wannan sojanefa ya saba dukan garadai kar ya illatamin yarinya mai biyayya." kai ya jujjuya mata tare da haɗe hannunshi wuri ɗaya ya mata alamun dan Allah kada ta fita ta barsu su tafi da ita. Shikuwa Ya Ameenu a zafafe yace. "Maza mu tafi gida ba ni zakiyiwa bayani ba." da sauri-sauri gudu-gudu tayi hanyar fita, kana shi kuma biyo ta. Suna ƙarasawa wajen motarsa ya buɗe tare da hankaɗata ciki, ransa amatuƙar ɓace ya ja motar sukabar ƙofar gidan. Gudu yake sosai hakan yasa cikin mintuna kaɗan suka iso G.R.A yana gama dai-dai-ta fakin ɗin motar, ya fito tare da zare belt ɗin wandonsa, ƙofar da take ya buɗe tare da figota waje, nan yashiga zuba mata belt ɗin ajikinta, kuka da ihu mai firgitarwa Zaleeha keyi tare da gudu ta nufi cikin gidan, kai tsaye ɓangaren Baban nata ta nufa. Tana shiga tafaɗa bayan Mamy dake tsaye acikin falon, gefe kuma Baba Malam ne zaune, sai kuma Ya Ahmad da kuma Mama wanda tacika tayi fam, ƙiris take jira ta fashe ta tarwatsa musu buhun bala'i. A harzuƙe Ameenu yashigo cikin falon, ganin haka yasa Zaleeha yin tsalle ta faɗa jikin Ya Ahmad ɗinta, ƙan ƙamesa tayi ƙam tare da ɓoye fuskarta a ƙirjinsa, kuka take sosai kamar ranta zai fita don sosai ya tsutstsula mata bel ɗin, Ya Ameenu na ƙoƙarin ƙara mata wani dukanne, Ahmad ya girgiza masa kai, alaman yabarta hakanan, da ƙyar Ahmad ya iya lallashinta tayi shiru, nan Baba Malam ya tambayeta ina take zuwa da bata kwana agidan aurenta?. Cikin matsanancin kuka tare da tsoro murya na rawa take cewa. "A garden nake kwana, Baba Malam wallahi ko ƙofar gidan ban taɓa fitowa ba , wallahi Baba Malam babu inda nake zuwa, a cikin gidan nake kwana." Sosai sukasha mamaki, amma sanin halinta da taurin kae irin nata yasa suka yarda cewa zata aikata hakan, a hatsale Habu yace. "To meyasa bazaki kwana cikin ɗakin kiba ko dai ƙarƙashin sirran aka nuna miki akace miki nanne ɗakin kwananki?." kai ta jujjuya cikin tsananin tsoro dan a duniya dai Zaleeha bata son abinda zai taɓa mata lafiyan jikinta murya na rawa tace. "Ni tsoronshi nakeji shiyasa nake fita woje." kai kawai Baba Malam ya jujjuya dan har ga Allah shi ya yarda Zaleeha tsoron takeji dan ya santa matsoraciyace bata son abinda zai taɓa lfyarta, kana kuma duk mace budurwa akwai tsoron namiji a ranta musamman in ance mijintane tofa akwai wannan tsoron da taraddin haɗuwar forko dana biyu wasu harma na uku. Wannan tunanin yasa Baba Malam yayimata faɗa tare da Nasiha, haka tayi kuka harta godewa Allah. Mama kuwa yau saboda tsaban ɓacin ran dake cinta kasa cewa komai tayi, tuni ma tabar musu falon, don idan ta tsaya zata iya dannawa Ameenu daya dakar mata ƴa ashar babu ruwanta da surkuntaka. Nan take Baba Malam yasa Mamy tashirya inda taɗauki Zaleehan ita da Ya Ameenun suka maida ita gidan su Saifuddeen, har gaban Ummi suka kaita, nan sukaiwa Ummi bayanin cewa wai agarden take kwana, nan sukaita bawa Ummi da shi Saifuddeen ɗin haƙuri, suka sa itama ta basu haƙurin nan su Ummi suka nuna cewa bakomai ya wuce, sosai Ummi taji tausayin Zaleehan ya kama zuciyarta, don kallo ɗaya zakayi mata kasan cewa andaketa, don ga jikinta nan duk yayi wani iri, sam Ummi bataji daɗin hakan ba. Nan Su Mamy suka kai Zaleehan har ɓangarenta, sannan suka ƙarayi mata nasiha, daga haka suka barta, inda takwanta tana meda numfashi, sosai takejin wani irin tsanar Saifuddeen ya ƙara ninkuwa acikin zuciyarta, ayanzu tanajin zata iyayi masa komai don baƙanta masa, domin akansa ne aka mata irin wannan azaban. Haka ranan dai ta wuni kuka , da yamma Belkeesu tazo nan tai ta ƙara zugata, hakama Mama ta kirata tai ta zageta wai me take jira da gidan tunda dai ba gidan ubanta bane to tabar musu gidan. Kada kuma ta bari wannan nakasashen ya rabata da budurcinta, harda cewa ta kwana duk inda takeso amman dai ta kare budurcinta. Koda dare yayi kamar kullum nan ta kwana cikin garden ɗin, shiko Saifuddeen yanzu abin natama dariya yake bashi, dan in gari ya waye ta fiti kamar ba itaba, shida kanshi ya yarda tana son ƴan uwanshi da Umminshi. Yau kwana uku da faruwan abun ,wanda yayi dai-dai da cika kwanaki goma da tayi a gidan, da yamma Adda Rahma tazo, duk da Raliya ta sanar mata komai amman sai takega kamar sharri sukewa Zaleeha dan yadda take nuna muso da kulawa. ita kuwa Zaleeha harga Allah har cikin ranta take son kowa na ahlin Saifuddeen ita dai shine bata so. Bayan anyi sallan ishane Ya Ahmad da Aunty Lubna suka zo gidan don sallaman Zaleeha dan gobe zasu koma Abuja, falon Ummi suka fara zuwa suka gaidata, kana Ya Ahmad ya bawa Ummi haƙuri akan ƙuruciyar Zaleeha, cikin jin daɗi da ganin dattakun yaron Ummi tace, "In sha Allah ba komai yarin tace." daga nan Saifuddeen yayi musu jagora zuwa side ɗinsu, sai dai kafinma su iso tuni Zaleeha ta tafi makoncinta, koda suka dudduba ɓata nan, sai Saifuddeen ya sanar musu inda taken, sosai ran ya Ahmad yayi matuƙar ɓaci, Auntƴ Lubna ce taje cikin garden ɗin ta kura ta, amman tasha jinin jikinta ganin yadda Aunty Lubnanma ta haɗe mata fuska, jiki a mace ta shigo, ganin ya Ahmad ɗinta ne yasa tayi saurin ƙarasawo cikin falon gefenshi ta zauna tare da manna kanta bisa damtsen hannunshi kawai sai ta saki kuka, abin mmki saiga Ahmad ya fara rarrashinta. nan yayi ta lallaɓata da yi mata nasiha da alƙawuran abubuwa masu daraja a rayuwarta yace. "Ni dai fatana da roƙona a gareki kawai kiyiwa mahaifinmu biyayya kada ki kunya tashi, ki zauna ɗakin mijinki ni kuwa babu abida bazan miki ba, ammanfa muddin kika saɓawa umarnin Baba Malam Zaleeha ki mance da cewa na sanki kin sanni. ki dena kwana a wojenan cikin ciyawin can, Zaleeha dame na rageki me ban mikiba na kayan ɗaki, ki gaya min in akwai abinda ban miki shiba in miki? ". Cikin share hawayenta tace. "Kamin komai Ya Ahmad ngd ." Kai ya jinjina tare da cewa. "To ki zauna ɗakin mijinki kiyi mishi biyayya ki bashi duk wani haƙƙinshi dake kanki." kai ta gyaɗa mishi a ranta kuma ceqa take. "Kayi haƙuri Ya Ahmad bazan iyaba." da haka dai suka sallameta suka tafi, inda Saifuddeen yayi musu rakiya har bakin motarsu, nan Ya Ahmad ɗin ya ƙara bashi haƙuri. To ranar dai Zaleeha a falonta ma ta kwana dan yanzu tayi shirin fara tarfa mishi rashin mutunci a cewarta sai ya saketa wanima bai saniba, sai dai kafinma ya dawo daga rakiyar su Ya Ahmad ta ɓingire tayi bacci, sabida sanyin ac da ƙamshi da tsabtan falon, koda yazo wuce kanshi ya girgiza tare da taɓe baki kana ya ɗan naga kafaɗunshi alamun babu ruwanshi da ita ya wuce side ɗinshi. Koda gari ya waye sai ta maida shirinta yau. Ƙarfe sha ɗaya da kwata na dare Saifuddeen yayiwa Umminshi saida safe black coffe ɗinsa, wanda Ummi ta haɗa masa ya ɗauka, tare da fita daga ɓangaren Ummin, sam ko kaɗan baiji tausayin Zaleehan nadaga abun da akayi mata ba, don shi sam baima fahimci cewa, an daketa ba. Kaitsaye part ɗinsu ya nufa, koda ya ƙarasa cikin falon nata, direct ɗakinta ya nufa dan yau wuni zumbur bai gantaba, haƙƙinta ne kuma a kanshi yasan halin da take ciki, kuma Umminshi ma ta umarceshi da ya shiga ya duba lfyarta, dan tunda tazo gidan bata taɓa fashin fitowa gaida Ummi safe da yamma amman yau tunda tazo da safe babu wanda ya kuma ganin fitowanta, sai dai Ummi tasa Raliya tazo har ɗakinta ta tambayeta lfya kuwa bata fitoba, to nan tace kanta ke ciwo, kuma hakan baya rasa nasaba da kukanda take yawanta yine a kwanaki ukun nan kuma ga dukan Ya Ameenu. A hankali ya nufi bedroom ɗinta   Ita kuwa Zaleeha zuwa lokacin harta zage zip ɗin rigarta inda take kwance akan gado, sosai takejin jikinta nayi mata wani irin raɗaɗi na musamman akan dukan da tasha yayi tsami a jikinta. Ƙarasowa cikin ɗakin yayi, tare da ɗan tsayawa ahankali yake ƙare mata kallo. Duk da kasancewar idanunta a lumshe suke, amma ba bacci take ba dan hawaye nata kwaranya daga idanun nata, jin motsin mutum acikin ɗakin, da kuma ƙamshin turarensa daya cika mata hanci yasanyata juyowa,  idanunsu ne suka sarƙe acikin najuna, da sauri tatashi daga kwancen da take, tare da ɗanja baya da alamun tsoronshi, takurawa tayi wuri ɗaya tare da sakin kuka, cikin rawan murya tace. "Dan Allah malam meya kawoka ɗakina?,Dan Allah ka fita, Ni tsoronka nakeji." Dubansa tayi duba irin mai cike da tsantsar tashin hankali da wahala cikin takaicinsa tasa tafin hannunta ta sharce hawayenta taso ta zuba mishi fitsara da tijara, sai kuma hakan ya gagareta sabida yayi mata kwarjii da yawa, gashi ya tsareta da manyan kyawawan idanunshi da suke da kwarjin mai tarin yawa madadin tayi masifa sai kawai ta tasashi a gaba taci gaba da kuka murya na rawa tace. "Dan Allah kaji tausayi na, wallahi ina sonshi bazan iya rayuwa da wani namijiba in ba shiba". kanshi ya tankwashe yana kallon yadda laɓɓan bakinta ke motsawa yana mai jin wani irin suya da ƙuna da zuciyarsa keyi, Ita Kumahakan da yayine ya tuno mata ashefa kurmane ma, cikin zubda hawaye tace. "Ayi mutum shi burinsa kawai ya raba masoya, ni bana son ko wani ɗa namiji sai shi, nace maka bazaka samu farin ciki daga gareni ba, saboda kai ƴan uwana suka tsaneni, saboda kai yau an wayi gari Ya Ahmad ma ya nuna zai iya tsanata sabida kai aka ɗaga hannu aka dakeni da sunan dukan dole in zauna da kai, am medani kamar jaka ko ganga abu kaɗan akama jibgata!." A hankali jiki na rawa turo da ƙafafunta ƙasa tare da miƙewa tsaye, hannuwanta tasa tana share hawayenta da wasu ke korar wasu, cikin kuka tace. "Ni dai ka fitamin daga ɗaki!." Taƙare maganar tana meyi masa nuni da ƙofar fita daga cikin ɗakin. Ganin ya kafeta da mayun idanunsa ne yasanyata ƙara jan baya kaɗan tace. "Waikai kam me yasa kake abu kamar mahaukaci ne da ina maka magana kana kallona, meyasa baka babbance so da ƙiyayya? Nace maka inada wanda nakeso". da sauri ya rumtse tafin hannunshi wai a gaban shi take ce mishi tanada wanda takeso tana matsayin matarsa. Ita kuwa cikin muryar kuka tace. "Tunda bazaka fitaba ai sai kayi ta zama kai in mun zauna ɗaki ɗaya ma me zaka iya min?, da idanu kaman na....." Batare da ta tantance ƙarasowarsa gareta ba, saiji tayi ansa mata ƙafa inda aka kwasota tuni tatafi su tafaɗa kan gado, cikin matsanancin ɓacin rai haɗi da rufewar ido, yasanya hannunsa inda ya jawota jikinsa, a harzuƙe yakama duka hannayen ta biyu ya, murɗe mata hannun nata yayi da ƙarfin gaske ya maidasu bayanta, hakan ne yasa tasaki wani irin ƙaran azaba,  sosai ransa ya ɓaci dajin kalamanta na kiranshi misaltashi da aikin mahaukaci, abinda Zaleeha bata saniba mutun ɗaya ya taɓa.mishi wannan furucin Iya Bukku kuma itama ya bata haƙwarenta a hannunta, idanunsa ne suka sanja kala inda sukayi jajur dasu, take jijiyoyin jikinsa suka mimmiƙe, sam idan akwai wani abu daya tsana to baiwuce zagi ba, zai iya tolereting komai amma banda zagar masa nasabarsa, haka kuma zai iya jure kowani zagi, amma koda wasa kada kayi kuskuren ƙiransa da sunan  mahaukaci. Azafafe yasanya hannunsa inda ya kamo ƴan ƙananun laɓɓanta, da yatsunsa biyu yasanya da ƙarfi ya shiga ɗana matasu akan laɓɓan nata da ƙarfi-ƙarfi, cikin matsanancin zafi haɗi da raɗaɗin da bakin nata keyi mata, tasaki wani irin kuka haɗi da ihu,  sam kukanta ko ihunta basu tsai dashi daga horar da ita da yake ƙoƙarin yi ba, sake matse bakinta yayi, yayinda ya sanya hannunsa inda yasake matseta ƙam, cikin kuka haɗi da masifar zafin da takeji tasoma jijjiga kanta, amatuƙar wahalce tasake sakin wani gigitaccen ƙara, tare da faɗin. "Wayyo Allah na bawani a kusane, ku taimakeni dan Allah, wayyo Ummi ɓarayi ɓarawo!." ina su Ummi ba jinta zasuyiba bare ta kawo mata agaji. Sake danneta yayi tare da sanya hannunsa ya murɗe lips ɗinta, tuni tanemi bakin ihu da kuka'n ta rasa, nan fa tasoma harba ƙafafunta tare da yarfa hannuwanta, zafin da takeji yakai zafi domin tuni idanunta sun fara fitar da sabin ƙwalla,  aƙalla saida suka ɗauki kusan mintuna 5 ahaka, sosai tafita hayyacinta kuka take kamar ranta zaifita, ido take jujjuya mishi da bashi haƙuri, "Wayyo dan Allah kayi haƙuri wallahi bazan sakeba." cikin ɓacin rai ya tureta kan gadon, kana ya rufa mata baya, rumtse idonta tayi da ƙarfi jin ya konto kanta, da sauri ta kuma buɗe idanun jin ya fincike rigar tata ya cillata gefe, tuni ƙirjinta ya baiyana irin bainar nan na ziraran miraran, ido ta zazzaro da ƙarfi jin tafin hannunshi kan breast, cikin wani irin kiɗima da farga ta riƙo damatsan hannunshi tuni jikinta gaba ɗaya tsuma yakeyi murya a hargitse tace. "Wayyo Allah na,na shiga uku dan ALLAH na tuba kayi haƙuri". Sai kuma taja wani irin dogon numfashi jin yadda yake murza ƙirjinta da sarrafa shi cikin tattauanawa tafin hannunsa, Wani irin kuka ta sake tare da yunƙurawa da niyar zata ƙwace kanta daga gare shi, sai kuma ta koma ta konta jin ya sake mata nauyi shi ƙafafuwan ta fara harbawa tare da jujjuya mishi kai kana tana ta kiciniyar kwace kanta. Shi kuwa Saifuddeen hannunshi ya ɗauke daga kan ƙirjinta kana ya danne hannayenta da taketa riƙe nashi hannu, sunkuyowa yayi ya manna bakinshi kan breast ɗinta na hannun dama, kana yasa hannunshi ɗaya ya haɗe hannayenta cikin hannunshi ɗayan, wasu irin abubuwan masu wuyar fahimta da misaltawa yakeyi suna shiga jikinshi da zuciyarshi karon forko a rayuwarshi da yake cikin wannan yanayi, wani irin sassanyan tsotsan kan nipples ɗinta yakeyi tare dasa hannu shine yana murza kan ɗayan. wasu tagwayen numfarfashi yake sauƙewa tamkar zasu fita da ransa gaba ɗaya jikinshi suma da karkarwa yakeyi, haka ya sashi sarrafa ta da zafi-zafi. Zaleeha kuwa ido ya raina fata, zufane yaketa tsastsafo mata duk ta inda hudan gashin jikinta yakeyi,kuka da ihu da magiya yakeyi tamkar zata mutu, tattaro sauran ƙarfinta tayi tasa janye hannunta ɗaya cikin zafin da takeji takai hannu kan hannunshi dake murza nipples ɗinta karo na forko a tarihin rayuwarta da namiji ya taɓa mata nononta, kai ta rinƙa jujjuya mishi ganin ya zuba mata kyawawan idanunshi da suka jiye zuwa kalan bacci-bacci, murya na rawa tace. "Na tuba dan ALLAH da sonka da manzon rahma ka barni bazan sake ba, na sani zaka iya min komai". Sai kuma hawaye car-car a hankali ya zame daga kanta ya koma gefe. Da sauri ta tashi zaune can gefe ta koma,hannunta tasa ta tallabi ƙirjin nata, sai kuma wasu sabbin hawayenta suka zubo sabida jin yadda nonanta ke zafi musamman bakinsu dan sosai ya tumurmusheta. da sauri ta janye hannunta tare da yarfa hannun tana mai zubda hawaye tare da fidda sautin. "Shhhhhhh wayyo zafi wayyo ka cinye min nona". wani irin kallo mai ɗauke da tsananin gargaɗi da alamun ki kiyayeni yayi mata, can cikin ransa kuwa dariya yakeyi ganin yadda yakeyi to wannan in an ratsa budurcinta sai yaya, haɗe fuska yayi tare da watsa mata mugun kallo kana ya wurgo mata rigar ta sannan ya yunƙura ya hau kekenshi, nan ya murza wheelchair ɗinsa kai tsaye ya fice daga cikin ɗakin. Wani irin ihu tayi tare da soma buga kanta ajikin bango, kuka take sosai da sosai, yayinda bakinta ke mata wani irin azababben raɗaɗi, har takai ga tanajin kamar ma laɓɓanta basa kan fuskarta ga nononta da sukayi jazir ɗan bakunan sai wani zut-zut sukemata babban tashin hankalinta in sunyi zut-zut ɗin nan har ƙasanta takeji canma yana mata wani irin abu mai sa tsikar jikinta miƙewa. ga hsnnunta da takeji kamar ya karya mata sune Kuka tacigaba dayi inda ta laluɓo wayarta tare da cewa. "Mugu kawai azzalumai zai cinye min nonona ya wani kamani yanata sha kamar ya samu tom-tom ya lallatse min abuna ya meyar min dasu second hand". kaitsaye ta dannawa Mamanta ƙira, bugu biyu kuwa maman ta ɗaga, jin kukan Zaleeha baƙaramin tayarwa da Mama hankali yayiba, cikin matsanancin tashin hankali Mama tace. "Ke Zaleeha yi shiru gaya min meya sameki? wani ɗan abu kazan ubanne ya ta ɓaki?." Cikin matsananci kuka na raɗaɗin zafin da laɓɓanta da nononta keyi mata tace. "Wayyo Mama zai kasheni, wallahi Mama bazan zauna ba, kasheni zaiyi dukana yake tayi tun ɗazu, nikam guduwa zanyi wallahi bazan zauna ba, shi ya dakeni kuma ƴan uwana ma su dakeni, Wayyo Allah nikam nashiga uku!." Zaleeha tafaɗi maganan cikin matsanancin kuka. Wani wawan shar mai tsada mama ta lailayo inda ta bankawa Saifuddeen shida gaba ɗaya zuri'arsa, cikin bala'i tace. "Narantse babu wani wanda ya isa, ya sake dukanke, kujimin hegen nakasashshe yaro mai jajayen kunnuwa ashe dama ya aureki ne don ya tozartamin ke,  wato dama ashe ba iya nakasa bace matsalar tasa harma da ciwon mugunta wato yaga zuƙeƙƙiyar yarinya yanaso ya lallatse min ke ko, to wallahi bazaki zauna ba, bai yiwuwa su su dakeki shima ya dakeki, sam ni ban haifi musu jaka ba, saboda haka nabaki umarnin ki gudu, maza ki tattara kayanki ki gudu Numan gidan Uncle Solomon, bankuma yarje kifaɗawa kowa inda kike ba, duk sai nayi maganinsu." Jin abun da Maman nata tafaɗa yasa Zaleeha tacika da murna, cikin kuka tace da Maman nata. "To." Ko kashe wayar bata tsaya yiba tashiga zuba kayanta acikin akwati, akwatuna 4 tacika da kaya, nan taɗauki duk wani abu nata mai amfani dake cikin gidan,   key ɗin sabuwar motar da Saifuddeen ɗin yasaya mata cikin kayan aure ta ɗauka, nan tafito inda ahankali take jawo akwatunan tana fitowa dasu,   babu kowa a compound ɗin gidan hakan yasa sauri-sauri tagama loda akwatunanta acikin mota, Kana ta koma cikin gida da niyar asuban fari zata bar gombe ta nufi Numan ta jihar adamawa, nan kuma ta ƙara yin mgna da Mama inda take ce mata ta bawa Zahira system ɗinta ta kawo mata da asuba. Haka kuwa akayi ana fitowa massalaci Sallan asuba ta, fito abinta kamar ko yaushe taje ta gaida Ummi to daga side ɗin Ummune ta wuce harabar gidan, tana zuwa ta shiga cikin motan tayi mata key,  maigadi ne ya buɗe mata gate ɗin gidan, cikin yanayi naɗan mamaki ya leƙa fuskarta wanda tayi caɓa caɓa da hawaye, aɗaɗare yace. "Ranki ya daɗe fita zakiyi ne?" Batare data basa amsa ba ta cilla hancin motar tata waje, gab ƙofar gidan taga Zahira na tsaye gefen keke napep, ita kuwa Zahira ganin Zaleehan yasa tayi sauri ta ƙarasa jikin motarta, system ɗin nata ta miƙa mata, da sauri ta amsa ta ajiye bisa kujerar baya, sannan suka ɗanyi wani mgn ƙasa-ƙasa kana ta danna hancin sabuwar motar dawani irin speed ta hau kan titi, gudu take sosai kamar zata tashi sama. Kana ita kuma Zahira ta shiga napep ɗin ya juya da ita. Ahmad ne ya bi motar Zaleeha da ido wanda duk abinda sukayi a kan idonshi dan fitowarshi kenan daga massalaci yaga Zahihara ta fito cikin napep tana raɓe-raɓe shiyasa ya koma gefen wani fulawa ya zuba mata ido. Saifuddeen Yana dawowa masallaci yau sai bai wuce side ɗin Ummi ba kasan cewar a makare ya tashi baiyi wonkaba ya wuce masallacin, shiyasa yanzun ya dawo side ɗinsu yafi son sai yayi wonka kafin yaje cikin gidan. Yana shiga side ɗin nasu ya nufi ɗakin Zaleeha dan ganin ƙofar a rufe yake, ɗan ƙwanƙwasa mata ƙofar yayi saida yaji a jikinshi duk baccinta ta farka sannan ya juya ya nufi falonshi. Yana barin bakin ƙofar ɗakin nata kai tsaye bedroom ɗinsa ya nufa. Yana shiga rage kayan jikinshi yayi kana ya wuce cikin Bathroom ɗinshi. kwance yake acikin  haɗaɗɗen jakuzzien wankansa ya hango haske mai yawa alamun tashin mota, take kuma saiyaji gabansa ya faɗi. "Hasbunallahu wani'imal wakil!." Yafaɗa a ranshi, sake maida kansa cikin jakuzzie'n yayi, lokaci guda tunaninta ya shiga yawo acikin ransa, sosai yayi mamakin yanda ta jure kwanan garden mai cike da sanyi da sauro da dai sauransu, wai duk dan kada yayi mata wani abu. Can gidansu Zaleeha kuwa, a fujajan Mama tanufi falon Baba Malam, suna zaune shida Ƴa Habu, da kuma Ya Ameenu, wanda yana fitowa masallaci ya taho gaida surkin nashi bappanshi kuma kamar yadda yakeyi wasu lokutansai Mamy. Ita ko Mama a hatsale ta banko labulen, babu ko sallama cikin tsananin masifa haɗi da bala'in dake cinta tace. "Dukkan ku hankalin ku ya kwanta, shikenan ni har abada kune zaku cigaba da nakasamin rayuwar ƴaƴa na, to shikenan saiku zuba ruwa aƙasa kusha, shidai mahaukacin da kuka aurawa Zaleeha yafara aikinsa, tunda gashi taƙirani tana kuka kancewa ya yi mata dukan tsiya, ko tashi bata iyayi, to wallahi bazan taɓa lamuntan haka ba, nidai kam ban aifawa wani ƙaton namiji jaka ba, dan haka wallahi dole sai ya sakarmin ƴata,  bai yiwuwa ku ku daketa sannan wani ƙato ma daga waje ya dake ta, wallahi tagama zama dashi kenan tunda dai yakai hannunsa jikinta, ban haifawa kowa jak!." Da ƙarfi ta faɗa bisa kujerar dake bayata sabida tsananin tsoro da firgitan da tayi da jin wani irin azabebben tsawan da Baba Malam ya daka mata. kame jikinta tayi tare da rumtse ida nunta gaba ɗaya jikinta rawa yakeyi tamkar mazari, kawai jira take taji ta inda zai r...! Littafina na kuɗine in kina buƙata turo katin mtn na 300 ta wannan number 09097853276 ko kimin transfer ta asusuna na 0005388578 jaiz bank Aisha Aliyu Garkuwa. By *GARKUWA'N FULANI* [9/9, 9:05 PM] +234 806 222 4030: *Wannan shafi nakine kyauta gareki kekyawar ƴar jaridar vison FM Gombe inai miki fatan al'khairi Zaleeha Babangida Hari mai shirin Babu Nakasasshe sai rago, dake da jonapwd gombe inai muku fatan al'khairi godiya ta musamman gareka malam ishaq* _ZAIBA MASU KARATU KADA KU SAKE A BAKU LABARI BIYA ƊARI 200 KACAL ki samu littafin Zaiba na Ummee Garkuwa littafi ɗaya maidarrusa da dama karanta Zaiba kisha dariya tausayi shauƙi bege ƙauna karanta Zaiba kisha barkwanci Sufi ga masu buƙata ku nemi Ummee Garkuwa 08037251895 ta wannan number_ Wani irin matsanancin farin ciki ne mai tarin yawa ya cika zuciyar Saifuddeen, haƙiƙa yau takasance rana ta mussaman agaresa ranan da bazai taɓa mantawa ba acikin ƙuɗɗin tarihin rayuwarsa, cikin ikon Allah yau gashi Zaleeha ta zamo mata agaresa, zata rayu cikin ƙarƙashin iko da damansa, zata zama itace aƙasansa ta tabbata matar nakasasshe, wani irin ƙayataccen murmushi kawai Saifuddeen ke sakewa, hakanan yakejin kansa dai-dai da kowani cikakken namiji,  cikin son tayasa murna Mutane suka dinga bashi hannu suna musabaha, kowa sai Allah yasanya al'khairi yakeyi masa,   haka yadinga amsar hannun mutane masu tayasa farinciki, hatta Ahmad da bawani son auren yake sosae ba yau yayi farinciki saboda auren Saifuddeen babban abune awajensu. Kasancewar al'adan ƴan Gombe ne yin receiption bayan an gama ɗaurin aure to hakanne takasance ga Saifuddeen domin kuwa tuni sun tsara haɗaɗɗen receiption wanda zasu koma gida shida abokansa da kuma wasu daga cikin jama'ar ɗaurin auren don suyi, haka suka shiga mota aka nufi gidan nasu Saifuddeen. Zazzafan zazzaɓine ajikinta har zuwa yau ɗin, yanzuma duƙunƙune take acikin blanket gaba ɗaya jikinta sai faman rawan ɗari yake, tun daga ɗakinnata tana iya jiyo sauti da hayaniyan mutane, wanda hakan shike ƙara affecting ɗinta, hartanajin kanta kamar zai rabe gida biyu, kwata kwata batason hayaniya,  turo ƙofar ɗakinnata akayi, Aunty Lubna da Maryam, da kuma ƙawarta Rashida ne suka ƙaraso cikin ɗakin, ganinta still a duƙunƙune cikin blanket yasanya su ƙarasowa daɗan sauri, Maryam ne taɗan yaye blanket ɗin tare da kai hannunta jikin Zaleehan nan taji zafi jau,  "Subahanallahi! dama bakida lafiya ne Zaleeha?". taƙare maganar tana me ƙara taɓa jikin Zaleehan. "Zaleeha!." Aunty Lubna taƙira sunanta, ahankali ta ɗan buɗe rinannun idanunta ta kalli Aunty Lubna'n, murmushi Aunty Lubna tayi mata tare da zama agefen gadon,  ganin haka yasa Zaleeha ta haɗo duka ƙarfinta tashi tayi taɗan zauna tare da jingina bayanta da jikin saman gado,  hannu Aunty Lubna tasanya ta dafa kafaɗan Zaleehan cikin kulawa da kwantar da murya tace. "Ki daina sa damuwa aranki Zaleeha, musamman a irin wannan ranan, yakamata ace yau kin aje duk wani makamen yaƙi da auren nan da kika ɗaura, sannan kin kori damuwa daga gareki,  ayanzu damuwar da zaki sa kanki bazai taimakeki da komaiba Zaleeha, babu amfanin wannan ƙuncin, yanzu lokacin da zaki bari zuciyarki ta huta ne, ayau kuma ayanzu an ɗaura aurenki da Saifuddeen, zaifi kyau ki rungumesa amatsayin miji bawai maƙiyi ba, saboda duk yanda kikakai ga ƙinsa, yanzu kin zama mallakinsa, zaki zauna aƙarƙashin ikonsa, yanzu komai zakiyi saida izininsa, saboda Allah yace girman miji ya zarce na iyaye, haka ku girmama mazajenku tamkar yanda zaku girmama iyayenku, harma fiye da haka, dan Allah Zaleeha kiyi haƙuri hakanan damuwar nan kibarta!." Aunty Lubna taƙare maganar cikin lallashi. Kuka Zaleeha tasanya tare da rumtse idanunta, wani irin ɗaci takeji amaƙoshinta, yayinda zuciyarta keyi mata zafi,  tabbas anyi mata abunda bataso, an aurar da ita ga wani ba mutumin da tafi so fiye da kowa ba,  take taji matsanancin tsanar Saifuddeen ya ƙara ninkuwa acikin zuciyarta, hartanajin zata iyayin komai don ganin ta nesanta kanta dashi, sannan kuma ta tozarta igiyar aurensa dake kanta, al'ƙawarine saita wulaƙanta aurensa, sam bazata zauna da nakasashshe ba!. Cike da tsananin tausayinta Maryam ta kamo hannunta, cikin yanayin sanyinta tace. "Zaleeha ke ƙanwatace, jini ɗayane ke yawo ajikinmu, tabbas inason duk wani abun da kikeso, haka kuma inaƙin abunda kike ƙi, saidai kuma Saifuddeen ba abun ƙi bane, irin Saifuddeen mata da yawa ke fata da burin samu amatsayin miji, kada ki taɓa dubansa da nakasarsa, domin NAKASA BA KASAWA BACE, haka kuma nakasa bata zama ciwo matuƙar ba nakasar zuciya bace, tabbas ina tayaki farincikin samun Saifuddeen, saboda inaji ajikina ko anan gaba koda bayan raina nasan cewa ƙanwata tasamu managarcin mijin dazai zame mata garkuwa, na tabbata koda ace yau kowa namu zai ƙare abarki ke ɗaya, bani da kokonto akan saifuddeen saboda nasan zai riƙeki da amana, bakuma zai taɓa bari ki wulaƙanta ba, nasan ayanzu kina ganin laifin Baba dama su Ya Ahmad da Ya Ameenu saboda sun aura miki wanda bakyaso." Ɗan tsagaitawa da maganan maryam tayi tare da sakin murmushi,  ahankali ta cigaba inda tace. "Watarana zakiyi alfahari da Baba Malam Zaleeha, zakuma kiji cewa yayi miki zaɓi irin wanda kowani uba ke fatan yiwa ƴarsa, tabbas nasani komin jimawa saikinyi al'fahari da zaɓin Baba Malam, sannan kuma kada kimanta cewar duk wanda yayi biyayya ga Iyayensa to har abada baya taɓa taɓewa." Duk wannan maganganun da Maryam keyi Zaleeha bata buɗe idanunta ba haka kuma hawaye basu bar tsiyaya daga cikin idanun nata ba,  zuciyarta tayi tauri, ɓacin rai ya cikata, tsana ƙiyayya masu tsanani, sun riga da sunyi tasiri acikin jikinta da ƙarfin sirin da Ruda ke zuƙa Mama suna banka mata, saboda haka babu wani magana daza a faɗa don atausasata da zaiyi aiki acikin ƙwaƙwalwa da zuciyarta, hasalima ji take kamar ana ƙara mata yawan tsanar Saifuddeen ɗinne. Duban Rasheeda Aunty Lubna tayi cikin kulawa tace, "Rasheeda kiyi abun daya dace, tasamu tayi wanka bari naje nakawo kayan da zata sa." "To" Rashida ta amsa zuciyarta cike da tausayin Zaleeha, saidai kuma ta wani ɓangare wautan Zaleeha kawai take gani. Su Aunty lubna na fita, Rasheeda ta kamo Zaleeha, da ƙarfi Zaleeha ta fusge hannunta daga na Rashida, cikin yanayi na faɗa-faɗa zaleeha tace. "kada ma kice zaki faɗamin komai Rashida, babu abun da zaki faɗa min wanda zan fahimta, sannan kowani kalma zaki faɗa, zakiyi asaran yawun bakinki ne kawai, dan koda wasa bazan taɓa ɗauka ba." Murmushi Rashida tayi tabbas tasan Zaleehan tana cikin ɓacin rai da baƙinciki, hakan yasama bazata biyeta ba, tasan tanajin haushinta ne saboda tabawa Saifuddeen da abokansa haɗin kai   wajen ganin antsara abubuwan biki sun tafi dai-dai. Dawowar Aunty Lubna ne ta lallaɓa Zaleehan inda ta haɗa mata ruwan wanka,  ko acikin toilet ɗin da ƙyar Zaleehan ta iyayin wanka, domin gaba ɗaya jikinta babu kuzari, tana fitowa daga wankan aunty lubna ta kamata inda ta zaunar da ita akan stull,  da ƙyar ta iya shafawa jikinta mai,  aunty lubna dakanta taɗanyi mata light meckup akan fuskarta kasancewar tasan ba isashshen lafiya bane da ita,  yimata meckup me yawa kaman takurata ne,  doguwar rigar bababar  atamfar chiganvy  me kalan ja aunty lubna ta bata tace ta sanya, kanta yafara ciwo sosai hakan yasa batayi musuba ta amsa, ta zura ajikinta, sosai ɗinkin rigar tayi kyau yayinda tabi jikinta ta lafe, rigar irin A shape dinnan ne me faffaɗan hannu, an ɗameta daga ƙirji zuwa ciki yayinda daga ƙasa kuma aka faɗaɗata, haka hannun rigar akayishi mai faɗi, sosai yayi wa Zaleehan kyau musamman ma idan ka haɗa da kalan atamfar da takasance ja mai ratsin green colour,   dogon gashinta da akullum yake cikin gyara aunty lubna ta tubke mata shi akusan wuyanta, jan ribbom aka maƙala ajikin gashin, aunty lubna dakanta tayi mata ɗaurin ɗan kwali mai kyau, hakannema ya ƙara ƙawata shiganta, kama daga kan sarƙa ɗankunne, harma da awarwaro.duka na gold aka samata masu kyaun gaske,  aunty lubna naƙoƙarin yafa mata mayafi ajikinta ta shagwaɓe fuska tare da turo baki, hawayene suka cika idanunta, ganin haka yasa Aunty lubna sakin murmushi tare da kamata ta kwantar da'ita akan gado,  komawa aunty lubna tayi tasanarwa da ya Ahmad halin da Zaleehan ke ciki, nan take Ahmad yayiwa family doctor ɗinsu waya, babu ɓata lokaci kuwa sai gashi yazo,  sanin cewa batason allura ne yasanya likitan bata magunguna bayan ya auna yanayin jikinnata, magunguna masu ƙarfi ya bata, tare da ɗaura mata drip, don kuwa shima zai taimaka wajen bata ƙarfin jiki da kuzari. Ko mintuna 20 ba ayi da samata drip ɗinba bacci ya ɗauketa. Acan gidansu Saifuddeen kuwa receiption aka gabatar me rai da lafiya inda akayi ɓarin nairori wajen ƙawata haɗaɗɗen abinci da drinks ɗin da akasha, bayan anci ansha ne kuma aka bawa kowa takeaway wanda ke ɗauke da kayan ciye ciye dana shaye-shaye, kowani ledan takeaway kaza ne guda aciki anyi raping ɗinta da poil paper abun dai sai wanda ya gani, nan fa Saifuddeen da abokansa suka shiga ɗaukan hotuna kala-kala,  haka sukayita bidiri basu suka samu kansuba saida aka ƙira sallan azahar nanfa masu tafiya masallaci suka tafi masu tafiya gidama suka tafi, inda wasu sun koma gidane don suɗan huta kafun lokacin ɗauko amarya da kuma diner. Gaba ɗaya gidan nasu Saifuddeen babu masaka tsinke, jama'ane takota ina, hatta ɓangaren saifuddeen dinma mutanene acikinsa maƙil. Su Ahmad da ishaq ne suke zaune afalon sunata hiransu, wasu kuwa na kallo, kowadai da abunda yakeyi, Saifuddeen na cikinsu inda gaba ɗaya hankalinsa kekan laptop ɗinsa, da alamun wani aiki mai tsananin mahimmanci yakeyi, dan gaba ɗaya hankalinshi na kan System ɗin gaba ɗaya idanunshi sai yawo sukeyi a jikin fuskar laptop ɗin, ganin hayaninyar abokan nashi yayi yawa ne suna katse mishi hamzarine ya sashi sarrafa kekenshin ya shiga bedroom ɗinshi. Abuja. Kuka sosae Amina keyi hakan tatashi yau batajin daɗi wani irin abune takeji ya toshe mata maƙoshi, tabbas babu makawa tasan kishin Saifuddeen ne ke ɗawainiya da zuciyarta, har wani zafi zafi takeji aƙirjinta, tanason Saifuddeen so mai tarin yawa tana kuma kishinsa sosai, bata san dacewa soyayyar Saifuddeen yayi ƙarfi azuciyarta ba sai yau daya kasance ya auri wata ba'ita ba,  ahankali take fitar da sautin kukanta, wayarta ta ɗaga tare da kunnawa, take hoton Saifuddeen wanda akayi masa ɗazu inda Hayatuddeen ya ɗaura a status ɗinsa ya bayyana akan fuskarta, don tuni ta sauƙe hoton zuwa wayanta, sosai yayi mata masifar kyau acikin farar shaddan dake jikinsa, fuskarsa ta ƙurawa ido, tabbas kowa yagansa yasan yanacikin matsanancin farinciki,   rumtse idanunta tayi tare da sakin wasu zafafan hawaye, tabbas ta barwa Allah itakam, ta fawwala masa dukanin lamuranta, tasan zaiyi mata jagora, idan tana darai da kuma rabo tabbas tasan watarana zata mallaki saifuddeen amatsayin mijinta. Kaduna, Asma'u Ahmad matawalle kuwa tun jinya da taga batun auren Saifuddeen sosai hankalinta ya tashi sai dai tasa a ranta babu wani na ƴa macen da zata hanata mallakar Saifuddeen a matsayin mijin aurenta, shiyasa daren jiya harda mafarkinta wai auren da ita aka ɗaura. Ahmad ne yabi bayan Ishaq da ya shiga bedroom ɗin Saifuddeen, akan gado suka sameshi, yana zaune kana abokinshi Aziz Wanda ya kasance babban SS shima yana zaune gefenshi duk sun zubawa laptop ɗin idanu bisa dukkan alamu wani abun Saifuddeen ke nuna mishi, kana da alamun tashin hankali a fuskarsu. Ahmad ne ya kalleshi da kyau kana ya zauna kan durowar gefen gadon, ganin hakanne yasa Saifuddeen gyara zamanshi kana ya jingina bayanshi da kan allon gadon. Wayarshi ya ɗauka text ya turawa Umminshi cewa yana jin yunwa kuma ya gaji. yana turawa ya ajiye wayar sannan ya ɗan miƙawa ishaq hannu suka yi irin gausuwarsu sanna ya kuma kalli Ahmad daketa mishi kallon tuhuma. Da Sallama Ummi da Adda Rahma suka shigo falonshi dake cike da abokanshi gaisawa sukayi sannan suka wuce cikin uwar ɗakan, yana ganin Umminshi ya ɗan kwaɓe fuska tare tanƙwashe kanshi bisa kafaɗunshi yayi rau-rau da manyan idanunshi da suke cike da tashin hankali da tarin gajiya, da sauri Ummi ta zauna gefenshi, murmushin jin daɗi yayi tare da raɓawa jikinta, hannnta tasa kan goshinsa sai kuma tayi saurin sunkuyiwa ta leƙa fuskarsa tare da cewa. "Meke damunka?." rumtse idonsa yayi da ƙarfi, sanna ya buɗesu, Adda Rahma kuwa murmushi kawai taketayi a ranta take cewa. "Hmmm shaleleln Ummi wannan ɗan shagwaɓan inaga randa duk ya kusanci matarma sai anyi jinya biyu mutun sam shi baya son wahala abu kaɗan sai yazo yayi ta narkewa Umminshi yana shogoɓa." a fili kuwa ajiye kulolin abincin da suka kawo mishi tayi tare da zama ƙasa kan carpet ta kamo hannunshi alamun tausasawa, sai kuma ta ɗan leƙo fuskar wayarshi da yake nunawa Ummi inda ya rubuta, "Ummi sacemin ita akeson ayi, meyasa? me tayi musu? wayake shirya sacemin matata ranar da za'a kawo min ita gidana? me nayi musu?." cikin kaɗuwa da tsoro Rahma ta mike tsaye tare da cewa. "Su waye ne Saifuddeen meyasa zasu saceta?." Ummi kuwa wani irin fargabane da tsoro ya rufeta jiki a mace ta kalli Ahmad da ishaq da Aziz ta musu bayanin abinda ya rubuta mata sosai Ishaq da Ahmad suka shiga ruɗani Aziz kuwa kai ya jinjina tare da cewa. "To ai da sauƙi tunda mun gano shirinsu, tun a zuwa ɗaurin aure Saifuddeen ya gano akwai baƙin ayarin motocin da suka shiga sahunmu kana ya ɗauki numbers ɗin motocin ya kuma bi diddigin inda aka sai motocin ashema a kamfanin Salisu ne, to yanzu bincike yazo mana da sauƙi dan Salisu ya bamu komai na masayin motocin harma da number wayarsa, shine ya bawa Saifuddeen damar bibibiyar kiran wayar dama motsinsu munji shirinsu na son sace Zaleeha." wasu siraran hawayenesu ka zubowa Ummi murya a raunace tace . "Aziz ku nemo hukuma a lamarin." kai Saifuddeen ya jujjuya mata alamun a a, shi kuwa aziz gyara zama yayi tare da cewa. "Uhmmm Ummi kenan to ai su kansu Hukumar Saifuddeen ne idonsu, tunda duk wani tantirin daya gagaresu gane inda yake Saifuddeen suke miƙawa aikin bin diddiginshi ta na'ura mai ƙwoƙwalwa yake gano musu komai, to yake binciko tantiran da basu shafeshi bama bare wannan dake son sace mishi amarya, yanzu haka ya tsara komai ya kuma haɗe kiran wayar waɗancan da wayata, yanzu haka hatta motar da ya saya dan ɗauko amaryarshi suma sun sayi irinta, dan su samu damar sacetan, rashin sanin Saifuddeen yana ɗaya daga cikin tawagar UPSC, ne ya sasuyin wannan gangancin." Adda Rahma kam gaba ɗaya hankaƙinta ya tashi, sai dai ganin yadda Saifuddeen ke basu ƙarfin guiwa yasa hankalinsu ya ɗan konta, Adda Rahman ne ta kalli Aziz tare da cewa. "Wacce tawaga ce kuma UPSC?." Cikin fidda nufashi yace. "Ma'ana tawagar Union public service commission! sai dai sirrance yake musu aikin, ƙarƙashin jagorancin DSS." Jinjina kai Adda Rahma tayi dan ta fahimci sirri Saifuddeen ke yi wanda ba'a cika son mutane su saniba, duk da sunsan yana tare da DSS amman basuyi zaton matsayin aikinshi ya kai nan ba. nan suka ɗan sashi yaci abinci sannan suka fita suka tafi. Ƙarfe 4 dai-dai kamar yanda al'adan gombawa takasance da yamma suke ɗauko aure kuma hakan ya samu asaline tun lokacin da ƙungiyar ƴan kalare suka fare da sace amare in za'a kaisu gidajen aurensu da dare shiyasa aka dawo da al'adar garin kai amarya gidanta da yamma ido na ganin idop. Hakan yasa gaba ɗaya abokan saifuddeen sun shirya tsab don zuwa ɗauko amaryarsu, motoci ne masu uban yawa suka tanada don zuwa ɗauko auren, tuni su Ahmad, Ishaq, Salisu, Wareesu, Saminu, Mudassir, Jabeer, Hisham, ibrahim, Rabi'u, Aziz, Aryan, Gaddafi,duk sun kammala komai, kowa yasanja shiga irin ta alfarma. Ahankali Saifuddeen yake tuƙa kekensa, har ya ƙaraso harabar gidan, sanye yake da ɗanyar shadda blue mai masifar kyau, sai shinning take yayi kyau matuƙa, saidai awannna karon baisanya gareba, hasalima rigar half jumper ce,  su Adda Rahama da suka fito don zuwa ɗauko aure tana ganin ƙaninnata taƙarasa garesa da sauri, yanaganinta ya sakar mata murmushi tare da shagwaɓe mata fuska kaman wanda zaiyi kuka,  murmushi Adda Rahama tayi tare da ƙarasowa ta shafa gefen fuskarsa, cike da ƙaunarsa tace. "To sakalallen Ummi na farko yanda naga ka shagwaɓe fuskarnan so kake kace kagaji ko? ehem ai duk wata shagwaɓa Hayatuddeen awajenka ya koyota." Murmushin daya bayyana fararen haƙwaransa yayi tare da ɗan lumshe idanunsa, hannunta ya kama inda ya ɗaura adai-dai saitin heart ɗinsa, dariya me haɗe da murmushi tayi, cikin jin daɗi ta dubesa inda tace. "Kamar yanda kake cikin farinciki Saifuddeen haka muma muke, farincikinmu nayau bazai misaltuba angon Zaleeha!." Yanzunkam dariya sosai Saifuddeen ɗin keyi saidai babu sauti, sosai maganan addan nasa tafaranta ransa, ganin yanda yake dariya yasa Adda Rahama lumshe idanunta tana mejin daɗi acikin ranta,  ita da kanta takoma bayansa inda ahankali take ɗan tura kekennasa, harsuka ƙarasa gaban wata hamshaƙiyar ƙatuwar mercedess benz 2019 mai azabar kyau da tsada, sabuwace dal sai shinning take tana ɗauke ido,  shida kansa ya shiga motar kamar yanda ya saba, inda Ahmad ya naɗe kekensa ya tura masa cikin both, nanfa kowa yashiga mota,  inda ƴan ɗauko amarya ma suka shiga tasu motar, ajere haka motoci ashirin da shidan ke tafiyan gwano akan babban titin, kasancewar Gombe akwai manyan tituna sannan kokusa babu ƙazanta akan gaba ɗaya titunansu, cikin motoci ashirin da shidan nan tsakiyarsu ta Saifuddeen take wanda cikintane za a ɗauko amarya. Tunda ta kwanta bacci ba ita ta tashiba sai 3:40 cikin ikon Allah kuwa jikinnata yayi sauƙi sosai don koda tatashi babu abun da takeji,  don taɗan samu kuzari ajikinta, still  Aunty Lubna da Maryam da Aunty Shatu ne suka tsaya kaida fata inda sukaga tasake sabon wanka,  to fa yanzukam meckup aka tsantsara afuskartata ta musamman,  kayan da tasa kuwa ya banbanta dana ɗazu, duk da kasancewarsu duka dogin riguna ne, saidai wannan na wani tsadadden shadda lace ne me matsifar kyau, shima ɗindai akwai ratsin ja ajikinsa, sosai yayi bala'in yi mata kyau, ɗauri ɗankwali aka zizara mata tare da yane mata jiki da babban mayafi, wasu tsadaddun sarka da ɗan kunne aka sanya mata, turare kuwa kusan ma wanka akayi mata dashi, don wani irin masifaffen ƙamshi take. Gefe kuwa Rashida da Balkeesu ne zaune, balkeesu sai washe haƙoran munafurci take, yayinda take ta saƙa sharri acikin zuciyarta, bakomai yasama tazo ɗaukan auren ba face matsanancin gulma dake cinta tana son taje taga gidan kurma gurgun tunda Mama ta hanasu ganin kayan auren kam. Cikin nutsuwa tarin motocin suka ƙaraso ƙofar gidan nasu Zaleeha, su Adda Rahama waƴanda sune zasu shiga gidan don fito da amarya suka fiffito, kaitsaye suka nufi cikin gidan. Shi kuwa Saifuddeen ido ya ɗan lumshe tare da yin murmushi ganin wata benzz irin tasa tazo kusa dashi ta tsaya kana yaga a ƙalla yanzu motocin sun kai talatin banda guda biyar wanda sukazo suka samu a cikin ƙaton harabar gidan duk da girman wurin saida ya tsuke ya musu kaɗan wata motar har tana gogar wata, lips ɗinshi ya ɗan lasa gano harda motocin masu sun sace Zaleeha ne a wurin. A cikin gida kuwa Aunty Lubna ce ta shiryata tsab inda ta rufe mata fuskarta da mayafin laffaya mai tsananin tsada da ƙyalli dake jikinta, Goggo Maryama ƙanwar Baba malam da Aunty Aisha ƙanwar Mama ce suka kamata harzuwa falon Baba Malam, inda Ya Ahamd, Ya Aminu, Malam Adam harma da Mamy ke zaune, nasiha sosai Baba Malam da yayunnata sukayi mata, inda suka gargaɗeta sosai akan zaman auren nata, nasiha sukayi mata irin mai ratsa zuciya da jiki, nasihace irin wanda ke nutsar da duk wata ƴa mace, saidai kuma ko kaɗan Zaleeha babu abu ɗaya data ɗauka daga cikin nasihartasu, hasalima kukan baƙinciki kawai takeyi, sukuma take suka cika da tausayinta domin kuwa duk atunaninsu nasihar tasuce ta tsumata har take kuka. Ganin kukan nata yaƙarune yasanya Aunty Aisha da goggonta ƙanwar Baba Malam suka kamata, domin kuwa tuni Maryam itama tasa kukan rabuwa da ƴar uwartata, haka Zaleeha take kuka sosai, yayinda ayanzu take kukan mai dalilai biyu, dalilin farko shine auren ta da aka ɗaura da wanda bataso, dalili na biyu kuwa shine dalilin dake sa ko wacce amarya kuka da zubda ƙolla tanajin bege da kewa da zafin barin gidannasu da zatayi, tabbas tasan zatayi matsanancin kewar yayu da ƴan uwanta, hakanan takejin duk ba daɗi, haka Aunty Lubna da Goggo suka riƙota har zuwa compound ɗin gidan, kuka take sosai, tanamejin tsananin baƙinciki aranta don kuwa kowani taku ɗaya da zatayi zuciyarta tafasa takeyi, yayinda wani irin malolon baƙin ciki ke cika zuciyarta, sosai takejin takaicin kaita gidan Saifuddeen da za'ayi. Haka suka nufi wajen motocin tare da tarin zugar ƴan rakiyar amarya wanda dama tuntuni su ake jira, Balkisu da Rasheeda ne tafe wanda dama mota ɗaya sukeson shiga da amarya, babuma kamar balkeesu don ita da biyu ma takeson zama kusa da Zaleehan, dan so take taƙara zugata sosae. a cikin motocin kuwa text Saifuddeen ya turawa Aziz na numbers ɗin motocin da suke zargi, amsa ya tura mishi da cewa. "Ba matsala duk nabisu na sace iskar tayun bayansu, sai ta motar dake kusa damu nan na barta amman naja tamu mutar na matsesu basuma da damar motsawa, na kuma gayawa Ahmad ya fito cikin motar taku yayiwa amarya jagora ,zakaga gefen hagu da daman ku akwai mata uku uku sojojine cikin farin kaya." murmushi mai cike da nasara Saifuddeen yayi. Shi kuwa Ahmad yana ganin fitowarsu yayi saurin ƙarasawa garesu, shiyayi musu jagora zuwa motar da za'a sanya amarya wato wanda Saifuddeen ke ciki, shida kansa Ahmad ya buɗe mata ƙofar motar, Aunty Lubna ne ta sata cikin motar, ganin Saifuddeen zaune acikin motar yayinda hankalinsa gaba ɗaya kekan laptop ɗinsa, yasanyata sakin murmushi, lallai tajinjinawa ƙauna irin na Saifuddeen da sauri ta kamo hannun goggo Maryama dake shirin shiga tace. "Tsaya Goggo angon yana ciki, shi yazo ɗaukan amaryarshi da kanshi." Ahmad ne ya ɗanyi murmushi tare da cewa. "Sabida tsarone babbar yaya ba don tsoro ba." dariya sukayi cikin happy Balkeesu ne tay kamar bata jisuba tasoma ƙoƙarin shiga motar, da sauri ta ɗan dawo da baya ganin Saifuddeen hakimce acikin motar haibarsa da kimarsa da kwarjinta sun bugi zuciyarta shakkarshi mai yawa ta rufeta, bisa ɗole taja da baya, Ya Ahmad da Adda Maryam ma dake gefensu murmushin jin daɗi sukayi sabida sunga tarin so da kulawar Saifuddeen a kan ƙanwar tasi, dan ya gayawa ya Ahmad duk abinda ke faruwa na son sace amarya, ya faɗa mishine da kashedin karfa wasu suzo su basu amarya su jira sai sunzo da kansu .Su Bilkeesu kuwa bisa dolensu suka shiga wata mota ta daban. Ahankali duka motocin ke tafiya a jere a jere. Sosai hankalin yaran Dalla yayi matuƙar tashi ganin duk motocin sun fice sun barsu sai nasu kawai ,nasun kuma duk sunyi faci, sai ƙwaya ɗayar nan, koda suka shaidawa Dalla hankalinshi yayi masifar tashi to waya gano shirinsu, waya ɓata mishi tsarin sace matar wannan gurgun kurman, dole a tsorace suka fita da motocin a haka suka lallaɓa suka isa wurin mai sa iska, yayinda duk abinda sukeyi Saifuddeen na ganinsu a system ɗinshi ta sanadin na'urar bibiya da ya bawa Hayatuddeen ya liƙa musu a jikin motar da take irin tasa. Tunda tashiga cikin motar ta cusa kanta atsakankanun cinyoyinta kuka take sosai har kaman zata shide, samma batasan dawa take tare ba acikin motarba, ta gefen ido yake kallonta, hakan ne ya tabbatar mishi kuka takeyi. Sosai yakejin kukan nata na taɓa masa zuciya da jiki dan jikinshi ya bashi kuka take ga kuma alamu yana ganin yadda ta takure tana shessheƙa, saidai kuma tun shigowarta motar ko ɗago kansa baiyi ba, gaba ɗaya ya maida idanunsa akan system na laptop ɗinsa, saidai kuma duka hankalinsa na gareta, ɗan ɗagowa yayi tare da numfasawa, cikin nutsuwa ya rufe laptop ɗin bayan ya saita abinda zai naɗe mishi diddigin yaran Dalla sai dai akasi kaɗan da aka samu lokacin da yasa yayi ƙarancin binsu har inda zasu isa, ido ya zuba mata cikin jin tausayinta yasan halinda mata kan shiga lokacin da suke barin gidan iyayensu zuwa gidan mazansu, dan bai mance auren Raihana ba da Adda Rahma ke badu labarin daga cikin gombe har suka isa Kaduna Raihana bata bar kukaba sai ta ɗanyi shiru sai kuma taci gaba har suna mata dariya wai hutawa takeyi bare da dama sun san Raihana saurin kuka gareta, ido ya lumshe tare da buɗesu ya zuba mata su, ahankali ya sanya duka hannuwansa akan kafaɗunta, ɗan ɗagota yayi kaɗan, ita kuwa Zaleeha jin anriƙe kafaɗunta ne yasanyata yin tunanin Aunty Lubna ce, hakan yasa batare data buɗe idanunta ba, haka bata yaye mayafin dake kanta ba, tafaɗa jikinsa, sakin sabon kuka tayi tare da sanya hannuwanta duka ta zagaye cikinsa, cikin kukan fitar hayyaci tace. "Dan Allah Aunty Lubna ku maidani gida, wallahi bana son barin gida,karku kaini cikin bare ban sansuba basu sanniba, wlh bana sonsa, natsanesa, ko ganinsa banason yi, mutuwa zanyi matuƙar kuka kaini gidansa, dan Allah Aunty ki taimakeni, taƙare maganar tana me cusa kanta cikin ajikinsa. Ahankali ya lumshe idanunsa, tare da sanya duka hannuwansa ya ƙara jawota jikinsa, wasu irin tagwayen ajiyar zuciya ya rinƙa sauƙewa take wani irin zazzafan shauƙi ya shiga ratsa zuciyarsa da jikinsa. Jin wani masifaffen ƙamshi mai azabar daɗin ji da shaƙa wanda bata taɓa jin irinsa ba na shiga cikin hancinta wanda ba ƙamshin Aunty Lubna bane yasanyata ɗan jan jikinta baya, ahankali ta ɗago kanta, azabure tawani irin jan jikinta baya, kallon fuskarsa da yayi masifar kyau wanda ita da kanta sauda ta ganshi kamar balarabe, ganin shinne yasanya komai ya ƙwace mata, wani irin baƙin ciki ne ya cika zuciyarta take tasaki kuka tare da maida kanta ƙasa, wani irin tafasa zuciyarta keyi mata. Ƙawataccen murmushi Saifuddeen yayi tare da maida bayansa ya jingina da jikin kujeran, lumshe idanunsa yayi yayinda yake shaƙan dadaaɗan ƙamshinta, runguman da tayi masa yasanya yaji wani abu na tsargawa ta cikin jikinsa, sam baiyi yunƙurin sake taɓa ta ba, haka kuma bai hanata kukan da takeyi ba, ahaka har suka iso cikin katafaren gidannasu. Nan fa ƴan kawo amarya kowa yacika da mamakin haɗuwar gida, masu son auren sai masha Allah kawai suketa cewa, Goggo Maryama ce ta riƙeta inda tace tashiga gidan da ƙafar dama haɗi da bismillah, ranta aƙuntace haka tayi bismillah duk da cewa bawai ganin gabanta takeyi ba, zuwa yanzu tama daina kukan, jira kawai take Saifuddeen yace da ita wani abu ta sauƙe masa kwandon bala'i. Baƙaramin mamaki kyan ɓanagaren na Zaleeha ƴan uwanta sukayi ba, don kuwa komai yayi harma ya zarcewa tunaninsu, koda Balkeesu taga uwar dukiyar da aka kashewa Zaleeha, dakuma irin tsaruwan gidan al'afarma part ɗin nata, saida taji wani abu kaman mashi ya caki zuciyarta, sam bata ɗauka haɗuwar wajen zaikai har haka ba. Acan cikin ɗaki aka zaunar da Zaleeha. Sannu ahankali jama'a ke watsewa don nan da wasu awanni za a gudanar da diner, Rasheda ma tatafi don zuwa taho da me meckup ɗin da zatayiwa amarya, hakanne yabawa Balkeesu daman ƙara hurewa Zaleehan kunne, sam tace da ita tadaina asaran hawayenta, tabari idan hidiman biki ya kammala plant ɗinsu da suka haɗa sai ya fara aiki, sosai Zaleeha kuwa tahau kan maganan na Balkeesu ta zauna wanda zugan bilkeesu da asirin mma yazo iri ɗaya. Kamar yanda al'adan Gombawa yake aduk sanda aka kawo amarya gidansu ango, to fa akan tarbesu da kayan ciye ciye dana shaye shaye, hakance takasance agidansu Saifuddeen dan kuwa sosai aka cikawa su Zaleeha kayan ciye ciye, komai cikin wadata akayisa, abun ma har mamaki yake bawa wasu daga cikin dangin Zaleeha don kuwa kuɗi sosae gidan su Saifuddeen ɗin ke kashewa wajen ƙawata komai nasu, kamar basajin ciwon kuɗin. Ya Habu kuwa da ya Aminu har cikin ɗakin suka shigo suka gargaɗeta akan batun diner muddin tayi abinda zai kunya tasu Habu yace. "Wlh rabaki gida biyu zanyi kin sanni ba mutun cine da niba, ni ba irin ya Ahmad bane." Dolenta ta nitsu koda suka tafi ko motsin kirki bata kuma yiba. Kasancewar ƙarfe 8:00 pm dai-dai za a fara gudanar da diner'n hakan yasa amarya Zaleeha tana idar da sallan isha aka soma tsantsara mata meckup akan fuskarta, musamman aka ɗauko ƙwararriyar meyin meckup inda tazo ta baje basirarta akan fuskar Zaleeha, wani irin haɗaɗɗen meckup aka tsantsara akan fuskar Zaleeha wanda yayi bala'in fito da kyawun fuskarta, dakanta ta zura wata haɗaɗɗiyar fitted weeding gown mai azabar kyau, jifa jifa aka sanya ratsin fari ajikin rigar, rigace irin doguwa ɗinnan wanda har sharan ƙasa take, sosai rigan takama jikinta tazauna ɗas, inda gefe da gefen waist ɗin rigar aka sanya wani irin yadi mai sharara wanda yake da masifar tsawo, haɗuwar rigar ya zarce misali, musamman ma yanda ya zauna ajikinta yayi ɗas, tabbas ko ba a faɗaba kallo ɗaya zakaiwa rigar kasan da cewa taja maƙudan kuɗaɗe wajen tsarata, haɗaɗɗen ɗaurin ɗan kwali irin na amare aka kafa mata akanta, bayan anyi parking dogon gashinta atsakiyar kanta, inda aka sanya mata wani haɗaɗɗen sarƙan gold mai tsananin kyau da tsada, dagakan ɗankunne har zoben dake hannunta duka na gold ne, masu masifar tsada da kyau, wani irin takalmi mai masifar tsini ta sanya aƙafafunta, bakaɗanba tayi kyau nafitar hankali, harwani ɗauke ido take, turare kuwa kamar ɓarinsa akayi ajikinta, sosai Zaleeha tayi kyau cikin shigarta ta diner, inda kowa ke yabawa da tsantsar kyawun da Allah yayiwa Zaleeha, ita kanta Zaleeha tasan cewa ayau ɗin tayi kyau. Gombe International Hotel Sosai aka ƙawata babban falon wanda ananne za a gudanar da diner ɗin, anyiwa wajen ƙawa naban mamaki tare da haɗaɗɗen decoration na peach and white, sannan kuma daga sama adon decoration blue akayi mai masifar kyau, gurin acike yake da jama'a , inda kowani team da kalan shigarsu, gabaki ɗaya abokan Saifuddeen shigar shadda blue colour ce ajikinsu, inda gefe guda kuwa su Hayatuddeen ke sanye da peach colour ɗin shadda, daga gefe kuwa su Adda Rahama suka tsantsara ado cikin wani tsadadden farin lace mai adon blue, gurin tuni yacika da jama'a zuwan ango da amarya kawai ake jira. Ɓangaren Zaleeha kuwa ana gama tsantsara mata kwalliya Rasheeda ta sanar dasu zuwan ango, hakan yasa aka ƙara ƙawata mata adon nata, Balkeesu da Rasheeda na riƙe da ƙasan rigarta dake jan ƙasa suka nufi compound ɗin gidan. Saifuddeen ne zaune acikin wata rantsatstsiyar mota yabala'in yin kyau acikin farar shadda mai peach colour ɗin aiki dake jikinsa, yayi kyau fiye daduk wani tunani mai tunani, idanunsane suka sauƙa akan tauraruwar amaryarsa wanda tsananin kyawun da tayi yaso zautar dashi. A hankali suke taku tamkar wahainiyoyi, suna isa gab ɓakin motar Saifuddeen ya...! Littafin nan na kuɗine in kika ganshi a woje to na satane kuma yaseeen doguwa aradu in kina buƙata turo katin mtn na 300 kacal ta wannan number 09097853276 ko kuma kimin transfer ta 0005388578 jaiz bank Aisha Aliyu Garkuwa. By *GARKUWAR FULANI* [9/9, 9:05 PM] +234 806 222 4030: *INAH ZAKI DAMU!!!* daga jin sunan labarin ba saikun tambaya ba kunsan labarine daya kunshi al'amuran da suke faruwa a cikin duniyar nan tamu wanda tunani ko zato bai taba kawowa ba, ban tausayi al'ajabi soyayya fad'akarwa da ilimantar wa duk zaku samu a cikin littafin nan da naira 200 kacal littafin marubuciyar nan da kuke nishad'antuwa da rubutun ta *SISIN MAMA* kada ku bari a baku labari dan samun mallakar littafin ku nemeta a wannan number d'in 08107499249. Aisha Aliyu Garkuwa: Sosai ta firgita da tsawan da Baba Malam ɗin ya daka mata, a zatonta zai kai mata dukane a nata banzan tunani kenan dan bashi yiwuwa namiji mai kamala da dottuku da tausayi ya daki matarsa, har sai irin dukan da shariya ta lamunce musu. Duk da Mama taci duka. Ganin yayi kwaffa ya jinjina kaine yasa ta Sake gyara tsayuwa ta, cikin rashin tunanin zuciya tace. "Tun wuri ma ku ƙira ku sanar dashi, ya sakomin ƴata, don wallahi bazan taɓa lamunta, haka nan ya dakar min ƴa ba!." Cikin matsanancin ɓacin rai da ƙunan zuciya Baba Malam ya kumadaka mata wata gigitacciyar tsawa wacce ta hautsine hanjin cikin Mama, saboda tsabar firgici  da kuma yanda tsawan yazomata abazata, saida tayi baya-baya inda ta faɗa kan kujera. Su Mamy da Ya Aminu kuwa, sosai suka shiga mamakin irin tsawan da Baba Malam ɗin yayiwa Mama wanda yake nuna zallan ɓacin ranshi,  saɗaf-saɗaf Ameenu da Mamy suka fice sukabar cikin falon. Cikin tsananin ɓacin rai Baba Malam yace da Mama.   "Ya'isa haka, kinyi min ba sau ɗaya ba, ba kuma sau biyu ba, duk ina ƙyaleki, to kisani ayanzu kin kai matakin da bai yiwuwa na ƙyaleki, sai yaushe zakiyi hankali ne? sai yaushe ne zaki samarwa kanki nutsuwa? sai yaushene ɗabi'ar musulamai da imani zai kama zuciyarki? ako yaushe idan kin tashi yin abunki bakya sa tunani acikinsa,  ashe rashin hankalinki har yakai ki tsaya akaina, gaban ɗana, ɗanki kuma surukin ki kina me ɗaga mini murya, to wallahi kisani daga yau na daina ɗaga miki ƙafa akan komai, badai zaman lafiya ne bakyaso ba, to shikenan zanbi dake aduk yanda kikeso. Sannan batun Zaleeha ki sani ƴata ce, ina da ikon da zansa ahukunta ta, aduk sanda tayi mini laifi, haka kuma  Saifuddeen mijinta ne, shima kuma yana da ikon da zai hukunta ta aduk sanda tayi masa laifi." Gyara zaman babbar rigarsa yayi tare da duban Mama cikin ɓacin rai da kuma tsanan halayenta yace. "Wallahi namiki rantsuwa Haleema aduk sanda kika sake, wata matsalar ta auku agidan auren Zaleeha, wanda har ya kasance da sa hannunki aciki, tabbas zan shayar dake mamaki,  tashi ki ficemin daga falo!!." Ya ƙare maganar murya a kausashe, kana yana meyi mata nuni da ƙofar fita daga falon. Cikin hanzari Mama ta-tashi inda ta fice daga cikin falon, duk da cewar tsawan da yayi mata ya tsorata ta sosai, amma hakan baisa ta daina cika da batsewan da takeyi ba, sosai tacika tayi fam, tana ƙarasawa part ɗinta ta saki dogon tsaki, tare da yin ƙwafa, abayyane tace. "Dani kuke wasan, ai dai nikam nawa ƙuncin kuma ya ƙare saura naku, yanzu ne aka fara buga wasan, sannan yanzu ne kuma tashin hankalinku zai fara, wallahi sai na shayar daku baƙin ciki, fiye da wanda kuka shayar dani". Tana ƙarasawa ɗaki, wayarta ta ɗauka inda ta dannawa number'n Ruda ƙira, bugu uku kuwa Ruda ta ɗaga wayar,  Mama na fitar da huci tayi mawa Ruda bayanin duk wani abu dake faruwa, shewa Ruda tayi tare da cewa. "Karki wani damu hankalinki badai kinsa ta gudu ba, shikenan ki manta dasu kawai, nan da kwana 2 zaki gansu arana karki damu kinji dai boka ya gaya mana zaisa ta daina jin tsoron ɓacin ran Babanta da son yimishi biyayya, kinji yace mana komai zai tafi yadda mukeso." Murmushin mugunta Mama tayi tare da aje wayar, kwanciya tayi akan gado, jin ranta takeyi fes, hakanan takejin kamar an rabata da ƙaya, domin kuwa tunda Zaleeha'nta ta auri gurgu, kullum kwanan duniya da baƙin ciki take kwana, yanzu kuwa Allah ya yaye musu, ya rabasu da masifa saboda haka ta gyara kwanciyarta donyin baccin safe, wanda ta ɗan kwana biyu bata yi shi ba. Can gidan su Saifuddeen kuwa, Ahmad na ganin tashin motar na Zaleeha'n, ya bita da kallo har sai da ta ɓacewa ganinsa, mamakin inda zataje awannan sanyin safiyan yake, yasan dai hakanan bazata fita da sanyin asuba ba kuma dai yasan hukunta bai ƙare ta koma wurin aikinta ba bare yace ko can ta sammakawa. Koma cikin gidan yayi, inda kai tsaye ya nufi ɓangaren Ummi, da sallama ɗauke abakinsa ya shiga cikin falon, zaune ya iske Ummi akan lallausan darduman dake shumfuɗe tsakiyar ɗakin, gefe kuwa Raliya ce, yayinda ummin ke jan carbin dake hannunta, ƙarasa shigowa cikin falon yayi, nan ya zauna abakin carpet ɗin tare, da ɗagawa Ummi gaisuwa, cikin girmamawa,  fuska ɗauke da murmushi Ummi ta amsa masa gaisuwan nasa, duban Ummin yayi tare da cewa. "Naga Zaleeha tafita yanzu, ko ta faɗa muku inda zata jene?." Ɗan jim Ummi tayi tare da cewa. "Tafita kuma, da safen nan?." Kai Ahmad yajinjina tare da cewa. "Yanzun naga fitarta." Girgiza kai Ummi tayi tare da cewa. "Ɗazun kuma tabar nan, don tazo ta gaisheni, saidai kuma sam bata faɗamin cewa zata fita ba, amma wata ƙila shi Saifuddeen yasan da fitarta." Kai Ahmad ya jinjina, tare da neman kawar da zancen ta hanyar duban Raliya, cikin kulawa yace. "Please haɗamin tea mana, yau so nake nafita da wuri." Da "To." Raliya ta amsa sannan ta tashi ta wuce kitchine, shi kuma kaitsaye ya wuce ɓangarensu don yin wanka. Can wajen Saifuddeen kuwa fitowarsa daga wanka kenan,  cikin nutsuwa ya gama goge jikinsa, inda ya sanya towel ya shiga tsane lallausan sumar kansa, wanda yaji aski irin na zamani, uwa uba yasha gyara sai ƙyalli yake, yana kammala goge jikin nasa, ya ɗauki body lotion ɗinsa mai daɗin ƙamshi, cikin nutsuwa ya shiga shafawa, yana kammala wa, ya shafe jikinsa da wani irin body oil spray mai matuƙar ƙamshi,  take gaba ɗaya ɗakin ya gauraye da ƙamshin sa,  ahankali ya tura wheellchair ɗinsa har zuwa gaban haɗaɗɗen drawer ɗinsa,  buɗe drawer'n nasa dake shaƙe da kaya yayi,  hannunsa yakai zuwa ɓangaren da ƙananan kayansa ke jere,   wani crazy combat jeans Black colour haɗi da wata D&G t-shirt mai kyaun gaske ya zaro, daga cikin tarin kayan nasa, sosai drawer'n nasa ke cike da kaya, sai kace wani kanti, wani kayan ma har mantawa yake dasu, dan ma duk bayan wani ɗan lokaci yana kyautar da kayayyakin da sosai musamman wa mutanen ƙungiyar su Jonapwd. Cikin yanayinsa na nutsuwa ya zura kayan ajikinsa, wanda suka matuƙar amsar farar fatarsa,  wani silver watch ya sanya ahannunsa, sannan ya buɗe wata ƴar glass drawer dake nan cikinsu yake aje caps ɗinsa, wata baƙar facing cap mai kyau ya zaro, inda ya ɗaura akansa, take yafito yayi wani daban dashi, ga wani irin kyau da yayi, ahankali ya tura wheelchair ɗinsa zuwa inda yake aje takalmansa, wasu flat shoe masu kyaun gaske ya zura acikin fararen ƙafafunsa, wayoyinsa da kuma laptop ɗinsa ya ɗauka, parfumed ya shafa, sannan yanufi hanyar fita daga ɗakin,  ahankali yake tafiyar da wheelchair ɗin nasa, har yasamu kansa acikin falon Zaleeha'n, ko ƙofar ɗakinta bai kalla ba haka yafice daga cikin part ɗin nasu gaba ɗaya,  direct ɓangaren Umminsa ya nufa. Kusan karo sukayi da Hayatuddeen wanda ke ƙoƙarin zuwa part ɗin nasu, ƙiransa shida Zaleeha akan cewa suzo suyi break, don su atunaninsu zuwa lokacin ta dawo. Duban Saifuddeen ɗin Hayatuddeen yayi, cikin ƙaunar Hamman nasa yace. "Wow Hammana kaga yanda kayi kyau kuwa!." Murmushi Saifuddeen yayi tare da duban Hayatuddeen, irin duban nan mai ɗauke da yanayin magana, alama yayi masa cewar. "Uhummm ." Kai Hayatuddeen yajinjina masa tare da cewa. "Fiye da kullum ma kuwa, wani lokaci Hamma nakan tambayi kaina, me yasa kai ba mace ba amma kowani kaya kasa saikayi musu kyau, saidai kuma idan na tuna da cewa Hamman nawa Namijin gaske ne, sai naji kaina ya ƙara girma, saboda samun ka amatsayin Hamma yafiyemin komai." Murmushin daya bayyana tsantsar kyawunsa yayi, cikin ƙaunar ɗan uwan nasa yasanya hannunsa inda yakamo kumatun Hayatuddeen ɗin. Dariya Hayatuddeen yayi tare da zagawa bayan hamman nasa inda ya turosa zuwa cikin falon, da shigowarsa cikin falon har falon ya ɗauki ƙamshin oud ɗin dake jikinsa. Har gaban dinning area Hayatuddeen ya tura hamman nasa,  inda Raliya da kuma Ahmad ke zaune, Raliya ne ta gaishe da yayan nata,  cikin ƙauna da kuma ganin ƙoƙarin ƴar uwar tasa na haɗa musu break fast kullum da takeyi ya amsa mata, yana tunanin gashi tasa an sallami mai akin wai duk a kanshi dan sun san yanada tsantsani.   Dai-dai lokacin Ummi ta fito daga cikin ɗaki, ganin Saifuddeen zaune yasa ta ƙara faɗaɗa fara'arta cikin kulawa tace. "Kunfito ko, ina Zaleeha'n, nace yau itama tazo cikin mu tayi break dan duk anzama ɗaya." Ummi taƙare maganar tana me jawo kujera ta zauna. Kallon Hayatuddeen Saifuddeen yayi, cikin body language yayi masa alama kan cewar yaje ya ƙirawo Zaleeha'n, kai tsaye hayatuddeen ya tafi don ƙiranta. Koda yaje part ɗin nasu, haka yayita knocking a ƙofarta, amma shiru, jin shiru ne yasashi tura ƙofar ɗakin ahankali, ɗan tsayawa yayi abakin ƙofa, da ɗan ƙarfi yace. "Aunty Zaleeha kizo muyi break, kin san dai bana iya jure yunwa." Jin shiru ba'a amsa shi bane yasanyashi ƙara kutsa kansa cikin ɗakin, nan yashiga dube dube kozai ganta amma shiru, kasa kunnensa yayi wai ko zaiji motsin ruwa a toilet, nan ma dai shiru, hakan yasashi juyawa kawai yafice daga ɓangaren nasu gaba ɗaya. Yana komawa yace musu baiganta ba, har ɗakinta ya shiga amma bakowa ciki,  fuska ɗauke da mamaki Saifuddeen ke kallonsa, to ina Zaleeha zata je kenan,  kallon Ahmad yayi wanda yake ƙoƙarin saving ɗin kanshi, yana cewa. "Maybe bata dawo daga fitan da tayi bane." Gane abun da Ahmad ɗin ya faɗa ne, yasa shi ɗan lumshe idanunsa,  Ummi ne ta dubesa, cikin kulawa tace. "Dama kasan da fitarta ne? dan Ahmad yace yaga fitanta tun da sanyin safiya koma ince asuba." Idanunsa ya rumtse tare da girgizawa Ummi'n kai, alaman "A'a."  ɗan jim Ummi tayi take kuma, wani tunani yazo mata inda ta raya aranta cewa ko gida Zaleehan taje, nan dai tace tasan cewa zuwa anjima zata dawo. Raliya ne tayi saving ɗinsu inda suka soma cin abinci cikin nutsuwa, shidai Ahmad hakanan jikinsa ya basa wani abu daban, yasan babu dalilin da zai kai Zaleeha gida awannan sanyin safiyan, idan da ace akwai dalilin ma to tabbas yasan da zuwa yanzu ansanar dasu. Haka suka kammala break fast ɗin nasu cikin nutsuwa, Ahmad ne ya miƙe dan yana so yaɗan fita, shikuwa Saifuddeen cikin falon na Umminsa ya koma, inda ya sauƙa daga kan kekensa, kwanciya yayi akan doguwar kujera tare da jawo laptop ɗinsa, ya ɗaura akan cikinsa, nan ya buɗe cikin nutsuwa yashiga yawo a internet, Hayatuddeen ma zama yayi akusa da hamman nasa inda ya jona game a tv plasma ɗin dake cikin falon, hakan yasa kowa da inda ya bada hankalinsa, Ummi kuwa ɗaki ta koma dan tanason kimtsa wasu kayyakin gudumowan biki da aka kawo mata, nan Raliya ta bita inda suka shiga aikin tare. Sosai yabada hankalinsa akan aikin da yakeyi, hakanne ma yasa har lokuta suka ja batare daya sani ba, inda Hayatuddeen kuwa tuni ya kwanta akan carpet yayinda bacci ya ɗaukesa, da dukkan alama jiya kusan kwana yayi yana chat, don abu ɗaya ne ke saka Hayatuddeen bacci da rana, shine idan bai samu enough bacci da dare ba, to dole da rana zaiyi bacci, wai abun ma yazo masa da sauƙi don yau basu da lectures sai ƙarfe 2:00 pm, shi yasama yaji gwamma yayi baccinsa, kafun time ɗin. Ummi ne tafito daga cikin ɗakinta, duban Saifuddeen tayi, ganin kaman baisan da zuwanta ba yasa ta shafi gashin kansa, ɗago da kansa yayi inda ya dubeta, ganin Umminsa ya sashi narke fuska,  akasalance yayi mata alaman sannu da fitowa, hakanan yake aduk sanda zaiga Umminsa, to fa raki da shagwaɓa kawai zai dinga yi mata, wani lokaci ko Hayatuddeen bai  kai Saifuddeen yawan shagwaɓa ba. Kansa Ummi ta shafa, cikin kulawa tace. "Inajin gabana yana ɗan faɗuwa tun ɗazu, ya kamata kaje ka duba Zaleeha kota dawo." Fuskansa yaɗan kwaɓe, tare da tashi zaune miƙa yayi inda yayiwa Ummin alaman cewa ya gaji, murmushi kawai Ummi tayi tare da ƙwala ƙiran Raliya, wanda ta shiga kitchine don ɗaura musu lunch, don a time ɗin kusan ƙarfe ɗaya ake nema. koda Raliya'n tazo, cewa da ita Ummi tayi, taje ta duba part ɗin nasu Saifuddeen ko Zaleeha ta dawo. Da "To." Kawai Raliya ta amsa, nan tafice daga cikin falon, koda taje part ɗin, haka tayi ta kwaɗa sallama amma shiru ba amsa, alaman bata dawo ba kenan,  haka ta fito daga falon, koda ta kawo compound ɗin gidan, parking space ɗinsu ta duba, nan taga babu motar Zaleeha'n, alaman kenan bata dawo ɗin ba, nan ta koma inda ta faɗawa Ummi cewa "Zaleehan bata dawo ba." Ɗan jim Ummi tayi nan tace. "To bari dai zuwa yamma, idan bata dawo ba sai muƙira gidansu mu tambaya, ko wani abunne ya faru." Shidai Saifuddeen ƙala baice ba, saboda ae Zaleehan bata maidashi miji ba, because da zata fita kanta tsaye ta fita, babu neman izini ba komai, wannan yasa shima bazai shiga cikin shirgin nemanta ba, sauƙa daga kan kujeran ma yayi, inda ya hau kan wheelchair ɗinsa, da kansa ya tashi Hayatuddeen, inda yace yaje ya ɗauro alwala yazo su wuce masallaci, don yin sallan Azahar, part ɗinsu yaje inda yayi alwala, koda yafito yasamu Hayatuddeen tsaye nan suka wuce masallacin dake kusa dasu. Ummi kam dai hakanan takejin wani abu dangane da tafiyan Zaleehan, sosai take fargaban abun da zuciyarta ke raya mata, aranta tana fatan ma Allah yasa ba hakan bane. Saifuddeen kuwa koda suka dawo masallaci, part ɗinsu ya nufa, nan ya nufi bedroom ɗinsa, inda ya kwanta ya ɗan huta. Abu kamar wasa tun ana ƙarfe ɗaya, biyu, uku, har zuwa ƙarfe huɗun yamma babu Zaleeha babu alamarta, sannan daga gidansu ba'a ƙira ance tana can ba, abun da yayi mugun ɗaga hankalin Ummi kenan, nan tatura akayi mata ƙiran Saifuddeen, zuwa yanzu yasake wanka cikin wasu tsadaddun riga da wandon jeans masu kalar navy blue, sosai sukayi masa kyau. Dubansa Ummi tayi cikin nuna damuwarta afili tace. "Gabana faɗuwa yake Saifuddeen, har yanzu fa Zaleeha bata dawo ba, kuma kace bata sanar dakai fitan ta ba." Kansa ya jinjinawa Ummin tare da kamo hannunta, cikin kulawa yayi mata alama da body language ɗinsa, kan cewar. "Kada ta damu Zaleehan zata dawo ne, wata ƙila tayi nisan zango ne." Girgiza kai Ummi tayi cikin kulawa tace. "Bari dai naƙira gidan nasu naji, ace mutum ya fita tun gari bai gama haske ba, kuma ace har yanzu kusan ƙarfe 5 ake nema amma baidawo ba." Nan Ummi ta ɗauki wayarta, inda ta danna wa number'n Mamy ƙira, don duk gidan number'n mamy kaɗai take dashi. Bugu biyu aka ɗauki ƙiran, amutunce suka gaisa da Mamyn, cikin nutsuwa Ummi tace. "Dama cewa zanyi ko Zaleeha na gidan naku ne, tun safe ta fita kuma shine har yanzu munji shiru bata dawo ba." Gaban Mamy ne ya faɗi, cikin  yanayin mamaki tace. "Tun safe kuma,  to ina take kenan don dai kam batazo gidan nan ba yau." Zuciyar Ummi ne ya tsinke cikin muryar damuwa tace. "Nima fargaba ne ya isheni shiyasa nace kawai bara naƙira na tambaya, indai ko bata gida to ina taje kenan, tunfa gari baigama haske ba ta fice." Cikin mamaki haɗi da fargaba Mamy tace. "Bakomai ku kwantar da hankalin ku, bari na shiga can ɓangaren mahaifiyarta ta saina tambaya kota zo, sannan zan faɗawa Baban nata ma, duk yanda ake ciki zaku jini." Nan Ummi tayi mata godiya, daga haka ta aje wayar,  kallon fuskar Ummi kaɗai Saifuddeen yayi, ya fuskanci cewa akwai damuwa. Mamy kuwa ko aje wayar batayi ba ta nufi ɓangaren Mama, da sallama ɗauke abakinta ta kutsa cikin falon Mama'n, Zaheera dake kwance tana kallo ne ta amsawa Mamy'n, dubanta Mamy tayi tare da cewa. "Zaheera ina maman taku." Zaheera bata kai ga cewa komai ba, saiga Mama tafito daga cikin kitchine, duban Mama Mamy tayi cikin nutsuwa tace. "Halima yanzun mahaifiyar Saifuddeen taƙirani, wai tun safe Zaleeha tabar gida kuma har yanzu bata koma ba, shine take tambaya ko nan tazo, nace da ita a'a, saidai kuma bansani ba ko tazo yau ɗin, naji ma kamar hankalinsu atashe yake, kuma gashi naga bata nan ɗin ma, ina Zaleeha tashiga kenan?." Mamy ta tambaya cikin yanayin damuwa. Tsuka Mama tayi tare da turo ɗan kwalinta gaba, cikin halin ko inkula tace. "Wani daga cikin ku yabani ajiyar Zaleeha ne da zakizo kina tambaya ta, ko kuwa idan tazo nan ɗin goyata zanyi abayana na kaita ɗaki na ɓoyeta, kwaje can kunemeta nikam banganta ba!." Mama taƙare maganar tana me yatsuna fuska. Shiru Mamy tayi tare da sauƙe ajiyar zuciya, ahankali tace. "Allah ya huci zuciyarki." Bata jirayi me maman zata ce ba, ta juya tabar falon. Ƙwafa Mama tayi tare da jijjiga kanta, cikin yanayin mugunta tace. "Gaba ɗayanku zaku sani ne, kuma ku sani, wallahi ƴata tagama zama da nakasashshe ehe." Daga ɓangaren na Mama kai tsaye Mamy wajen Baba Malam ta nufa, tana shiga kuwa ta iskesa zaune shida Habu da kuma Ameenu, cikin nutsuwa Mamyn ta sanarwa Baba Malam abun dake faruwa, nan take Baba Malam yaji zuciyarsa tayi wani irin bugawa, gyara zamansa yayi tare da fuskantar Mamy'n cikin, nuna damuwa yace. "Zaleeha bata gidan mijinta kuma, to ina tashiga?." Rumtse idanunsa yayi, tare da ambatan sunan ALLAH Acikin ransa, haƙiƙa Zaleeha kyautace daga wajen Allah, amma sosai lamuranta ke caza masa ƙwaƙwalwa, sam batajin magana ko kaɗan ta bambanta da Maryam. Ya Ameenu kuwa wani irin baƙin cikin Zaleehan ne ya turnuƙesa, shikam tun ba yauba ya gane cewa iskanci Zaleehan keji dashi, yayi rantsuwa kuma saiya sauƙe mata, guguwar dake kanta, burinta kullum shine tajawo musu abun faɗa, so take ta ɓata musu suna, ta kuma ɓatawa Baba Malam halin dattakon sa. Ya Habu ne yace. "To yanzun ina taje?." "Sai Allah!." Mamy ta faɗa asanyaye. Nan take Ya Habu ya ɗauki wayarsa, inda yasoma ƙiran ƴan uwansu na kusa ko Zaleehan taje, amma babu wanda yace tazo. Ya Ameenu ne ya ƙira Maryam awaya inda ya tambayeta ko Zaleehan tazo bayan fitowan sa daga gida, cikin tsananin tashin hankali Maryam tace masa bata zoba. Baba Malam da kansa ya ɗauki wayarsa inda ya dannawa ƙanwarsa, wato Goggo Maryama ƙira, nan ma cewa tayi sam Zaleehan bata zoba, haka Ya Habu da Ya Ameenu suka dinga ƙiran layukan ƴan uwa da kuma abokai na kusa, waƴanda suke  tsammanin cewa Zaleehan zata iya zuwa, amma babu wanda yace tazo, ko labarinta ma babu wani wanda yace yaji. Take Ya Ameenu ya danna ƙiran Lambarta, haka wayar tayita ringing har ta katse, no answer, sake dialing yayi, still har ƙiran yasake katsewa ba a ɗauka ba, saida yayi mata 4 missed calls, amma duka no answer, Ya Habu ne shima yaƙira layin nata, nan ma bata ɗauka ba, sau 5 yana ƙira amma shima bata ɗauka, Baba Malam ne dakansa ya laluɓo lambar tata, nan ya danna mata ƙira, saidai shima kamar sauran haka har ya katse no answer,  nan fa akeyinta ran Ya Ameenu idan yakai million to saida ya ɓaci, take yasoma sakin huci, yayin da yakejin wani ɗaci aransa, har wacece Zaleeha da baba Malam zaiyi mata 2 missed call amma bazata ɗaga ba, lallai idan ya kama Zaleeha, saiya rabata gida biyu. Ganin duk bata ɗauki wayansu bane, yasa Mamy ta ƙirata da layinta, duk dai abu ɗayane bata ɗagawa, nan hankalin Mamy yatashi, take tsoro ya shigeta, nan ta fara tunanin ko Zaleehan bata lafiya ne. Ya Ameenu ne ya kirata da sabon SIM ɗinsa, inda ya sake dialing number'n Zaleeha'n, shi ɗin ma dai batai picking ba, maida wayarsa cikin alj'ihu yayi, inda ransa ke ƙara tsuma yana ɓaci. Baba Malam ne ya dubi Ya Ameenu, nan yace. "Yaje gidan su Saifuddeen ɗin, don sanar dasu halin da ake ciki, idan kuma yasamu Zaleehan ta dawo, to ya basa umarni ya tattakata yayi mata duka irin wanda sai ta kasa tashi, sannan kuma ta faɗa masa gidan ubanwa taje." Nan Ya Ameenu ya miƙe, haka ya fita yana huci don cika umarnin Baba Malam ɗin. Acan gidan su Saifuddeen kuwa, sosai Ummi ta ɗaga hankalinta, tabbas tasan zuwa yanzu rashin dawowan na Zaleeha ba lafiya ba,  ita da Raliya harma da Hayatuddeen gaba ɗaya hankalinsu atashe yake, Adda Rahma wanda itama yanzu zuwanta, jin labarin rashin ganin Zaleeha'n , sosai ya tashi hankalinta. Saifuddeen kuwa yana zaune afalon, laptop ɗinsa yake ta dannawa, sam baikula da harkan neman Zaleehan ba domin duk wani motsinta afa tafin hannunshi take yasan muddin ya maida na'urarshi kanta bata da mafakar da zata shiga ya gaza ganewa.   Zuwan Ya Ameenu ne ya ƙara tada hankalin su Ummi,  nanfa abu kamar wasa ya zama gaske,  sosai aka shiga neman Zaleeha amma kamar ɓatan laya babu ita babu alamanta, Ahmad da Ya Ameenu ne suka shiga mota, inda suka soma zaga gari nemanta, har gidansu Rasheeda da Bilkeesu sunje, amma sun shaida cewa basu ganta ba, nan Ya Ameenu yasa Ahmad dake driving suka nufi family hause ɗinsu, wato gidansu Ya Ameenun kenan, nan ma dai bata nan,  gaba ɗaya ƙanne da yayyan Ya Ameenun saida yaƙirasu ko Zaleehan tazo amma haka suke cewa bata zoba, sosai hankalin familyn ya tashi, Zakariyya da Ziyada kuwa da labarin neman Zaleehan ya iskesu, haka suka shiga damuwa sosai, Hajja kuwa take tasoma kuka, abunka da tsufa, dama kuka baiwa tsofi wahala. Gaba ɗaya ran Ya Ameenu yasake ɓaci, domin sosai shida Ahmad sukayi buji-buji dasu wajen neman Zaleehan, gashi yanzu har ƙarfe goman dare kenan amma babu ita babu alamanta, still wani abun baƙin cikin kuma shine idan anƙira wayarta bata picking,  koda kuwa za'ai mata ƙira ashirin ne bazata ɗaga ba, wannan dalilin yasa ran Ya Ameenu dana Baba Malam ƙara ɓaci,  can gidan su Saifuddeen kuwa, sosai ɓatan Zaleehan ya ƙiɗima Ummi da su Raliya, Saifuddeen kuwa, ganin yanda hankalin Umminsa ya tashi sosai ne, yasan yashi barin sashin na Ummi gaba ɗaya, part ɗinsu ya koma inda ya kwanta yayi shiru, sosai al'amarin Zaleeha ke ƙona masa rai wani lokaci, sai dai yayi rantsuwa bazai taɓa bari sha'anin haukanta ya damesa ba, wani abu can daban bai damesa ba, saboda haka haukan guduwanta bazai taɓa damunsa ba, yasani koma tana inane to ita takai kanta, sannan kuma ita ta zaɓa, abinda dai ya sani yasa a ransa ta boni da aurensa dan babu saki a tsarin rayuwarsa ta gama guje-gujenta aurensu takalmin kazane mutu ka raba ya rantse wa ransa ko shekara 30 zatayi bata dawoba ba saki ta shiga ukunta dashi dan babu ita babu wanda take cewa tana son. Can gidan Baba Malam kuwa, sawa yayi aka ƙira masa Mama, cikin tsananin ɓacin rai ya dubeta, ransa nayi masa suya yace. "Zaleeha tabar gidan mijinta tun asuba, sannan har yanzu bata dawo ba, an kuma nemeta an rasa, tabbas nasan cewa kome Zaleeha ta aikata da sa hannunki, saboda haka ina kika kaita kika ɓoyeta?." Yaƙare maganar murya a kausashe. Ihu Mama tasanya tare da zamowa ƙasa ta zauna daɓas, hannu tasa aka, cikin ɗaga murya tace. "Innalillahi wa'inna ilaihirraju'un! wayyo Allah na, shikenan kun cuceni kun halakarmin da ƴata, shikenan abun danake gudu shiya faru, baƙin cikinku yasa ta gudu, wayyo Allah na!!." Mama taƙare maganar tana me rushewa da kuka,  kuka sosai take tana faɗin,  "Shikenan kun cuceni, kun rabani da ƴata, wayyo Allah Zaleeha na!." Kallon takaici Baba Malam yayi mata tare da girgiza kansa kawai,  nan ya wuce zuwa ɗakinsa, don baida wadataccen lokacin da zai tsaya sauraran ihun Mama'n. Ganin Baba Malam ya wuce ɗaki, sannan Mamy da Habu sun fice daga falon ne, yasa Mama saurin tashi, cikin matsanancin farinciki tayi juyi, fes takejin zuciyarta, nan ta sake sakin kukan ƙarya, haka tafita daga falon na Baba Malam tana ta faɗin, cewa sun cuceta, tare da cewa lallai su nemo mata ƴarta duk inda ta shiga ta fita. Awannan rana kuwa har ƙarfe 2 na dare babu wanda ya rumtsa  acikin waƴannan gidaje guda biyu,  Mama kuwa da gangan tahana idanunta bacci, hakanan taketa kukan cewa ane mo mata Zaleeha'nta. Saifuddeen kuwa, damuwar dayaga Umminsa aciki ne kawai ya hanasa bacci, sosai yayi ƙoƙari wajen bawa Ummin nasa baki, amma ina Ummi har ƙwalla saida ta zubar, musamman ma idan ta tuna da cewa, basu san wani hali Zaleehan ke ciki ba, shi kuwa Saifuddeen tsab yaga text ɗin da Zaleeha ta turawa ƙawarta Bilkeesu cewa ta gudu, sabida ya haɗe kan wayar Zaleeha da tasa duk abinda zatayi zai gani kuna zaiji, to dai har yanzu baiga ko ji ga inda ta nufaba. Ɓangaren Baba Malam kuwa, baƙin ciki da ɓacin rai ne suka hanasa bacci, tabbas yaji ajikinsa cewa, ba ƴan kidnappers ko wasu mutanen bane suka kama Zaleehan ba, hakanan yaji ajikinsa cewa, guduwa kawai tayi don nuna masa cewa bai isa da ita ba, sannan tayi hakanne don ƙara masa damuwa, sannan ta kuma watsar masa da mutumcinsa a idanun jama'a. Ya Ameenu kuwa tsananin takaicin Zaleehan ne ya hanasa bacci, yayinda Maryam kuwa ke kuka wiwi, rarrashin duniya yayi mata amma takasa daina kuka. Ya Ahmad ma da ba'a gari yake bama, yanacan Abuja saida yakasa rumtsawa, wani irin babban tashin hankali yasamu kansa aciki lokacin da aka faɗa masa, haka ma Aunty Lubna, sosai hankalin Ya Ahmad ya tashi, don yasan cewa Baba Malam zaisanya damuwar acikin ransa, ko kaɗan kuma baya ƙaunar abun da zai taɓa mahaifinsu. Haka dai gaba ɗaya ahlin gidaje biyun nan sukayi kwanan zaune, dasu da kuma duk wani danginsu na kusa,  washe gari kuwa da sassafe Ya Ameenu da Ya Habu suka sake bazama neman Zaleeha. Inda Ahmad ma yashiga cikinsu,suka shiga nemanta tare. Baba Malam kuwa da sassafe ya shirya, inda ya nufi Dukku, dan zuciyarsa na raya masa cewa ko can taje. Haka su Ya Ameenu suka ƙarishe yawonsu amma babu Zaleeha babu alamarta, nan Ya Habu ya shiga motarsa, kai tsaye  ya nufi Ɓilliri, wajen dangin mahaifiyarsu, koda zai sameta acan, amma koda yaje haka yagama shan wahala, ko ina yaje, sai suce bata zoba. Baban Mama kuwa ranshi yayi masifar ɓaci duk da kasan cewarshi kafuri baiji daɗin abinda Zaleeha ta aikataba, koda yake ya zargi ƴarsane a lamarin, dan a zahiri ta nuna mishi bata son auren. Can Dukku kuwa Baba Malam babu inda baije duba Zaleeha'n ba, kama daga gidajen ƴan uwa da abokan arziki, duk yaje amma babu ita ba labarinta, sosai hankalinsa ya tashi, nan take yaji wani ciwon kai mai zafi ya rufesa, alaman cewa jininsa ne keson hawa, don dama yana da ciwon hawan jini. Ya Ahmad kuwa tuni ya biyo jirgi shida Aunty Lubna, inda suka dira acikin garin Gombe, sosai hankalinsa ya ƙara tashi ganin cewa har yanzu ba'aga Zaleehan ba, ƙira kuwa yayi mata yafi sau hamsin amma bata ɗagawa ba, wannan abun shiya ƙara jefasa acikin tashin hankali. Ɓangaren Zaleeha kuwa tun da ta ɗauki hanya bata tsaya ba harsaida tasamu kanta acikin garin Numan na Adamawa yola,  gaba ɗaya ƙiran da akeyi mata akan idanunta, amma zuciyarta tayi wani irin nauyi wanda batajin zata iya ɗaga ƙiran kowa, sannan kuma batajin cewa zata kashe wayarta. Hamdala taketayi a ranta tanaga ta tsira daga farmakin Saifuddeen, dan yayi masifar razanata da bata tsoro jiya da dare, hannu tasa ta share hawayenta wanda bata san dalilin zubowarduba a hankali tace. "Ya Allah kasa kada Babana yayi fushi sani". Ajiyar zuciya ta sauƙe tare da cewa. "Hmmmm Allah na godema daka tsere tar dani daga hannun wannan mutumin, na sani tabbas da na ƙara kwana a gidan shi, haka zai ta lallatseni kamar maggoro yayi ta tsotsini kamar tom-tom daga nan zai gwada min ƙarfin yace zai farkeni, dole nema in gudu daga komarshi mugu kawai." haka dai taci gaba tuƙi. Daga cikin garin na Numan, kai tsaye anguwar bakin kogi ta nufa, don acanne uncle solomon ɗin yake, a bakin kogi nan sukeyin rayuwa,  da ƙyarma ta iya ƙarasawa wajen, don kafun ma ta isa tuni tayi laushi, amatuƙar gajiye takejin kanta,  a ƙofar ɗan madaidaicin gidan wanda gininsa yayi masifar tsufa ta dai-dai-ta parking ɗin motar, buɗe murfin motar tayi inda tafito kai tsaye tanufi cikin gidan, ko damuwa da mutanen dake kallonta batayi ba. Sanincewar su ɗin ba musulmai bane yasa, kanta tsaye ta kutsa kanta cikin gidan. Elizabet  matar Solomon dake zaune atsakar gida tana tatan markaɗen dawan burkutunsu, jin motsin shigowan mutum yasa ta ɗago kanta ta dubi ƙofar shigowa gidan, ganin Zaleeha tsaye yasanya taɗan saki fuskarta, cikin ɗaga murya Elizabet ɗin tace. "Solo oya come out ga baƙuwarka ta iso." Solomon dake cikin ɗaki jin abun da Elizabet ɗin ke faɗa yasan yashi fitowa, hannunsa riƙe da fartanya, da'alama dama gona zashi, kasancewarsa manomi kayyakin marmari na bakin kogi. Ganin Zaleeha yasashi washe haƙoransa. Cikin gurɓatacciyar hausarsa yace. "Aa Zali'a kin iso kenan, your wellcome, shigo ciki  mana." Ɗan guntun murmushi Zaleeha tayi tare da ƙarasowa cikin ɗan ƙaramin gidan,  tana wucewa Elizabet ta bita da kallo ƙasa-ƙasa ta taɓe baki. Nan Zaleeha tabi Uncle ɗin nata zuwa cikin ɗaki, inda yace da Elizabet ta kawo mawa Zaleehan ruwan sha. Abakin wata katifa wanda ta fara lashewa Zaleehan ta zauna, nan shima Uncle ɗin nata ya zauna. Dubansa tayi tare da cewa. "Good evining uncle, haw was the day?." "Am very fine my daughter, how are you, i hope are you okay, right?." Murmushi ta ɗanyi tare da jinjina masa kai, ahankali tace. "Yeah." Dai-dai lokacin Elizabet ta shigo hannunta ɗauke da kofin ruwa wanda ta tara a bakin fomfonsu dake ɗan tsakar gidan nasu, aje kofin tayi agaban Zaleeha, ɗauke kai Zaleeha tayi domin sam batason jin ƙamshi ne ko warinsu zata ce ne oho, cikin ƙasa da murya tace. "Aunty good evining." "Evining, how are you?." Elizabet tafa ɗa tana me kallon Zaleeha'n, wanda take ta faman ƙarewa ɗakin kallo. "Am fine!" Zaleeha tafaɗa tana me ƙarewa kofin da aka kawo mata ruwa aciki kallo, Allah Yasani itakam ƙyanƙyaminsu takeji, hakanan take ganin komai nasu yafita daban, komai nasu ba irin na sauran mutane ba, shiyasa ma kwata kwata bata fiye shiri da dangin mahaifiyarta ta ba, domin ita sam batason zama da su, saboda zama da waƴanda hasken addinin musulunci bai cimmusu ba, sai ahankali, zakaga kwaɓa da kuma shirme kala-kala. Duk da kasancewar tanajin ƙishin ruwa, amma kasa shan ruwan tayi, don sam bata yarda ma da tsabtan gidan ba. Hira kaɗan suka ɗan taɓa da Uncle din nata, nan yace da ita zai tafi gona, yana tafiya ta jawo akwatunanta, zanin gadon dake kan katifan da take kai ta yaye, nan taciro wani bedsheet mai ɗan taushi wanda baida nauyi ta shumfuɗa, kimtsa akwatunanta tayi agefe kana ta fito da sallayanta da komai na buƙatan musulmi ta a dana, hand bag ɗinta ta zuge, nan ta ciro wasu diary milk chocolate guda biyu, tare da wani cake, nan ta kwanta tare da jawo wayarta, power bank dinta ta ɗauko inda ta saƙala wayarta a charge, kwanciya tayi tana mecin chocolate ɗin ahankali, hakanan dai ta gwammace gwara zaman nan dana gidan SAIFUDDEEN dake cike da jin daɗin daular duniya. Acan Gombe kuwa, Haka su Ya Ameenu suka ƙare yawonsu har suka gaji, dawowa gida sukayi inda sukayi jigum jigum. Baba Malam ma haka ya dawo daga Dukku zuciyarsa duk ba daɗi. Ganin yanda gaba ɗaya dangin suka tashi hankalinsu ne yasanya wani tunani ya faɗowa Ahmad, nan yaƙira Ya Ameenu yasanar masa cewa, lokacin da Zaleeha zata tafi, tabbas yaga Zaheera tazo a napep inda ta bata wani abu a jaka, sannan ita Zaleehan tatafi, ita kuwa Zaheera ta shiga napep din daya kawota, saboda haka atambayi Zahira ko tasan inda Zaleehan taje. Habawa ae Ya Ameenu kaman kububuwa haka yaji ransa ya ɓaci, atake ya gayawa Baba Malam, nan Baba Malam yace da Zakariyya wanda tun safe yake gidan, cewa yaje ya ƙira masa Zahira, Zakariyya na zuwa ƙiranta, Mama ta buga tsalle inda ta kama hannun Zahira, tare da cewa tare zasu je, nan Mama tace da Zahiran ko kasheta zasuyi, kada ta sake tafaɗi inda Zaleeha take, dayake Zahiran ma zuciyar arna gareta, take ta kafe kan cewa bazata faɗa ba. Atare suka shiga falon ita da Mama, cikin zafin nama Ya Ameenu ya damƙo Zahira, wani lafiyayyen mari ya sauƙe mata akan fuskarta, take tafasa wani uban ƙara, tare da buga tsalle tasoma yayyarfa hannuwanta, cikin zafin zuciya yace. "Ina Zaleeeha ta tafi?." Bata iya basa amasa ba saboda marin ya matuƙar gigitata. Cikin fushi haɗi da ɓacin rai Mama tace. "Maganar banza ma kenan, wannan ai kora kunya da hauka kuke ƙoƙarin yi min, ku da kanku kuka salwantar min da rayuwar ƴata, sannan yanzu kuzo kuna tambayan Zahira, wallahi Ameenu kakiyaye ni kada kasake ka ƙara kai hannunka jikin Zahira tam!!." Mama tafaɗa ranta amatuƙar ɓace, zuciyarta kuwa cike da fargaban kada zafin mari yasa Zahira faɗin gaskiyan inda Zaleeha take. Ran Baba Malam a ɓace ya dakawa Mama tsawa, cikin faɗa yace. "Ina ki ka kai Zaleeha?." Afusace Mama tace. "Bansan inda takeba!!." Cikin ɓacin rai Baba Malam yace. "Na baki nanda kafun gari ya waye, duk inda Zaleeha tashiga ki tabbatar kin dawo da ita ɗakin mijinta, idan kuwa ba haka ba, ki tattara komai naki kibarmin gidana, kuma sannan idan kin tashi tafiya ki haɗa da Zahira karkiyi kuskuren barmin ita agidana, don bana ƙaunar zama da munafuki!, kada ki manta koki ƙira Zaleeha ta dawo ko kuma kibarmin gidana ayu basai gobe ba!!!." Yana gama faɗin haka ya wuce ɗakinsa, amatuƙar fusace. Wani irin masifeffen tsorone ya rufe Mama kadafa Baba Malam ya saketa ta koma ƙauyensu noma, wani sashin na zuciyarta kuwa zugar ruda ce ta ratsota haka yasa ta ɗan ja tsaki tare da kamo hannun Zahira, cikin ɓacin rai tace. "Mu tafi ai nima inada gidan uba, saboda haka kwana ɗaya bazamu ƙara ba, Zaleeha ne kuma bamusan inda take ba, kuma ko sama da ƙasa zasu haɗe, aurenta da nakasashshen gurgu ya ƙare kenan har gaban abadan." Littafina na kuɗine in kin gashi a wojema na satane. Turo katin Mtn na ɗari 300 kacal ta wannan number 09097853276 ko ka/koyi min transfer ta asusuna na 0005388578 jaiz bank Aisha Aliyu Garkuwa kana ki turo min shaidar biyan ki.    By *GARKUWAR FULANI* [9/9, 9:05 PM] +234 806 222 4030:                              "Wai Duk wannan haɗe fuskan na memene wai? dan ance za'a ƙara maka aure?." kanshi ya sunkuyar ba tare da yace komaiba. Ahmad ne ya gyara zama tare da duban Saifuddeen ɗin, cikin zolaya yace. "Manya kenan angon mata biyu, gaskiya bakowani namiji bane zai taki sa'a irin wanda ka taka, auren mata biyu awata ɗaya kacal, lallai Saifuddeen kai ɗan gata ne." Harara Saifuddeen ya watsa Ahmad ɗin tare da haɗe fusks, wani irin abu yakeji a maƙoshinsa, sam shi atsarinsa babu auren mace wanda ta wuce sama da ɗaya a rayuwarsa. Ummi ne ta ɗan saki murmushi tare da duban Ahmad, cikin kulawa tace. "Ni kaina naji na gamsu da batun ƙarin auren Saifuddeen, amma kuma sai-dai bansan wace kalar matar kuma zai ƙara samowa ba, musamman ma yanzu da yace babu wata wacce ya keso." Murmushi Ahmad yayi cikin nutsuwa yace. "Saifuddeen ai mai farin jini ne, muna nan zaune zamuga wata santaleliyar budurwa ta bayyana, don neman aurensa! In wata ta gudu wata zata zo. Ita kuwa ɗiyar taki Zaleeha in taga dama tafi ruwa gudu." ya ƙare maganar yana  gimtse dariyarsa, don sosai yakejin wani irin farin ciki yau ɗin, don yasan ta hanyar ƙarin auren Saifuddeen ɗinne kaɗai Zaleeha zata shiga cikin sense ɗinta kuma tanannne Saifuddeen zai samu nitsuwa. Cin ƙufula Saifuddeen ya ɗauki ɗaya daga cikin pillow kujerun falon, nan ya wurgawa Ahmad ɗin, da sauri Ahmad ya kauce yana dariya,   duban Raliya dake zaune Ahmad yayi, cikin son ƙara tsokar Saifuddeen ɗin yace. "Nikam zan fita, idan na fita kuwa sai inda mai na ya ƙare, saboda zan zaga gari, ko Allah ma zai sa na samawa ɗan bazawarin abokina mata ta biyu!." Yanzun kam harta Ummi saida tayi dariya, shikuwa Saifuddeen sake kwaɓe fuska yayi nan yasake wurgawa Ahmad ɗin pillow, da sauri Ahmad ya kauce kana ya fice daga cikin falon yana murmushi. Ahankali ya danna madannin wheelchair ɗinsa, inda ya ƙaraso har gaban Ummi dake zaune,  Raliya kuwa miƙewa tayi inda tabi bayan mijinta. Hannun Ummin Saifuddeen ya kamo, karyar da wuyansa yayi, tare da shagwaɓe fuska, narai-narai yayi da idanunsa, tare da ɗan yaɓe lips ɗinsa, hakan yasa yanayinsa ya koma kamar na ƙaramin yaro,  ganin yanda yayi da fuskar ne yasa Ummi fuskantar me yake nufi, cikin yanayin lallashi ta kama hannunsa, tausasa murya tayi tare da cewa. "Nasan bakaso amma haƙuri zakayi ka ƙara auren nan Saifuddeen, tun da dai kaga shi baban Zaleehan da kansa ya faɗa, kuma ai dai nasan kafahimci me yace, tun da dai yace akan maganar ƙarin auren,  ba shawara yake ba ka ba, umarni ne." Kai Saifuddeen ya ɗan girgiza, tare da ɗan lumshe idanunsa, kana ya buɗe su alokaci guda, duban Ummin nasa yayi, cikin body language ɗinsa yake yi mata alaman cewa. "Bashi da ra'ayin ƙarin aure, sam babu auren mata biyu atsarinsa, idan ma ya ƙara auren ya zaiyi da matar?." Kanshi ta shafa cikin bashi ƙarfin guiwa tace. "Je kasha maganinka, daga gobe zamuyi mgnar, kana Kayita Addu'ar Allah ya tabbatar maka da al'khairi a cikin lamarin." Kanshi ya gyaɗa mata cikin bin umarninta ya juya ya nufi side ɗinshi. Ita kuwa ta koma cikin ɗakinta zuciyarta fal farin ciki, Adda Rahama ta kira ta sanarwa abinda ke faruwa, abinda yayi matuƙar faran ta mata rai, nan tace. "In sha Allah zanzo in ya Adnan ya barni." "Allah ya kaimu." cewar Amin Amin ta amsa kana sukayi sallama. Washe gari da yamma, Saifuddeen na zaune gaban Umminshi cikin nitsuwa yake mata tambayar meyasa zata bari aƙara mishi aure bayan tasan shi mai raunine. Wani irin yalwataccen murmushi Ummin tayi tare kamo hannunshi, bata kai ga basa amsa ba. Adda Rahama wanda tun ɗazun ta shiga kitchine haɗo wa kanta abun da zata ci, ta dawo cikin falon, zama tayi tare da duban su Ummi'n. Nan Ummi ta sauƙe ajiyar zuciya tare da duban Adda Rahama'n, cikin kulawa tace. "Kinjisa wai shi bayason wani ƙarin aure, waishi mai raunine." Dubansa Adda Rahama tayi cikin kula tare da ɗan nutsuwa, cikin son fahimtar dashi tace. "Akan maganar ƙarin auren nan, ba wai zaɓinka aka nema bafa, zaɓin da aka baka dai kawai shine ka fito da wata, wanda kake ganin ta kwanta maka arai, amma ƙarin aure kasa aranka cewa in sha Allah babu fashi, ita wanda kake mutuwar so ɗin ba guduwa tayi daga gareka ba, saboda haka nidai ina goyon bayan da kasakeyin wani auren, don gaskiya bazamu barka kaci gaba da zama ahaka ba." Fuskarsa ya haɗe tare da dubansu su duka biyun, cikin body language ɗinsa, yayi musu alaman cewa. "Ahakanne zai ƙara aure bayan ko yaushe bisa keke yake, kodai sun manta cewa shi ba cikakken lafiyayye bane, ko kuwa sun manta da cewar shiɗin mai rauni ne, ayanda yake ma gaskiya baijin zai iya zama da mata biyu." Murmushi Adda Rahama tayi tare da tasowa, ta ƙaraso inda yake, hannunta ta sanya inda ta dafa kafaɗunsa, cikin ƙauna haɗi da tausayinsa tace. "Ni na tabbatar kai ba rago bane, nasan zaka iya rayuwa da mata huɗu ma ba biyu ba,  kai jajirtaccen Namiji ne Saifuddeen, saboda haka kada kabari rauni ya ziyarci tunanin ka, tun ada kai jarumi ne, haka ayanzu ma kai ɗin, you are the super hero, sannan kafi kowa sanin nakasa bata taɓa zama kasawa, sai-dai ga wanda ya bari zuciya da kuma tunaninsa suka mace, saboda haka ako yaushe kasa azuciyarka cewa, kai ɗin jarumi ne!! Sai dai kuma in salon tirjiyarka ce hakan". Taƙare maganar tana me ɗan bubbuga kafaɗunsa tana murmshin zanca wai shi mai raunine kaji yaro da wayo wato ace bazai iya jure mu'amala da mata biyu ba. Shiru yayi tare da lumshe idanunsa,  hakan na nufin cewa kenan bashida wani zaɓi? ko kuwa dai ƙaddaransa ne take ƙoƙarin canzawa? Ganin yayi shiru ne yasa Adda Rahama komawa kan kujera ta zauna, nan ta shiga cin abincinta hankali kwance. Da sallama Hayatuddeen ya shigo cikin falon Ummi, ganin su azaune ga kuma Hammansa daya haɗe fuska, yasan yashi ƙarasowa cikin falon, jakar makaranta da kuma littatafan dake hannunsa ya watsa akan kujera, zama yayi daɓas akan sofa, tare da miƙe ƙafafunsa, cikin shagwaɓa haɗi da kasala ya ɗago indo ya dubi Ummi, asangarce yace. "Ummi am so tired, ƙafana bayana kaina idona kunennena ɗuwawuna kai ko'ina ɗina ma ciwo suke min!." Murmushi Ummi tayi, tare da cewa. "To sannu auta na, ae dai ku kam gaba ɗayan ku haka kuke, abu kaɗan ke gajiyar daku, sai kace ba gwaraza ba." Sake shagwaɓe fuska yayi, cikin salon sakalci yace. "Wallahi Ummi makaranta ba daɗi, duk acika ku da lectures, yau fa ko ɗan hutu bamu samu ba." Ƙare maganar yayi yana me ɗago kansa, inda ya kalli Saifuddeen, wanda ya haɗe fuska, inda ya kawar da kansa gefe, da'alamu cewa ba ya cikin yanayi me daɗi, cikin kulawa haɗi da faɗuwar gaba, asanyaye Hayatuddeen ɗin yace. "Hamma!." Kasancewar Saifuddeen ɗin ya juyar da fuskarsa, zuwa wani ɓangare na daban hakan yasa baiji ƙiran da Hayatuddeen ɗin yayi masa ba, don dama sai yana kallon ka ne, sannan yake karantar abun da kake faɗa, ta hanyar kallon yanayin motsin bakinka shiyasa yake da yawan kallon ammanfa ga wanda yake son ya gane abinda zai faɗa. Ganin Hamman nasa baisan da cewa yanayi ba, hakan yasa ya taso da sauri ya, ƙarasowa gaban Hamman shi hannunshi ya ɗaura a akan kafaɗan Hamman nasa, ahankali Saifuddeen ya ɗago da kansa, duban Hayatuddeen ɗin yayi, sai kuma ya kau da kansa gefe. Hakanne yasa jikin Hayatuddeen yayi sanyi sosai. A take kuma yaji gabansa ya faɗi, ƙirjinsa ne ya shiga duka, cikin zuciyarsa yace. "Nashiga uku badai Hamma na yasamu labarin cewa, yau na fita amakaranta, na bi Khamis muntafi yawo ba?." Cikin ɗari-ɗari da fargaba ya kalli Ummi, wanda ke ƙoƙarin tashi, don komawa ɗaki, da sauri ya rufa mata baya, jin mutum abayanta yasata juyowa, kafe Hayatuddeen ɗin tayi da ido, tare da cewa. "Lafiyanka ƙalau kuwa kake biye dani, sai kace wani ƙaramin jariri, kodai ka aikata wani rashin gaskiya ne?." Ummi tafaɗa tana me ƙare masa kallo, don tsab tasan yaranta, da zaran sunyi wani abun da ba dai-dai ba, takan saurin ganewa, ko daga halin rashin nutsuwa da zata gansu aciki, kamar dai yadda ta fara zargin yanayin canji nitsuwar Hayatuddeen. Ƙifi-ƙifi Hayatuddeen ɗin yayi da idanunshi tare da cewa. "A'a babu abun danayi, kawai dai naga ran Hamma Saifuddeen ne kamar aɓace yake." Ajiyar zuciya Ummi tayi tare da cewa. "Hmm rabu da Hammanku, gata ake son a mishi shi kuma wai baya so." Da sauri yace. "Ummi wanne irin gatane?." murmushi tayi tare da cewa. "Wai fushi yake don ance masa ya ƙara aure, shine yake ta faman haɗa rai sai kace wanda akace yayi wani abun, wanda ba dai-dai ba." Cikin zaro ido Hayatuddeen yace. "Haaah Ummi to kuce ni inyi auren mana, tunda shi baya son gatan ni kuyi mini." Cikin mamaki da al'ajabi da zazzaro ido Ummi tayi kana tayi kasake tana kallonshi da nazartanshi. Shi kuwa da sauri ya dawo nitsuwarsa gudun karta ramfoshi. Ajiyar zuciya mai ƙarfi Hayatuddeen ya sauƙe, ya godewa Allah da yasa, ba asirinsa bane ya tonu, domin yasan tabbas idan Hamman nasa, ya gane irin abubuwan da yake yi, to fa kashinsa ya bushe, yasan sai anrabasa da duk wani abu nasa najin daɗi. Gyara tsayuwarsa yayi tare da cewa. "To Ummi me yasa zai ƙara aure, yaushe ma yayi auren?." Harara Ummi ta watsa masa, tare da cewa. "To kai mekasani acikin aure da kake tsoma baki cikin abun  da babu ruwanka?." Kanshi ya jujjuya tare da cewa. "Wallahi ba abinda na sani, kawai a auro mishi mai sonshi tunda hegiyar nan taƙi zama." haɗe fuska Ummi tayi tare da cewa. "Hayatu baka da kunya fa ba yayarka bace kake ce mata hegiya, to a kul wlh kada in sake jin ka zagarmin ƴata dan mu dai Zaleeha bata ƙi muba bata mana wani laifiba ita dai auren ne da bata so." Murmushi yayi tare da ɗan shafa kansa yace. "Afwan ya Ummi bazan sakeba, nima nasan Zaleeha na sonmu amman dai ina jin haushinta in na tuno wai bata son Hamma nane yasa ta gudu." ya ƙarishe mgnar tare da, juyawa ya inda ya fice daga cikin ɗaki, a falo ya samu Adda Rahama, har yanzun Saifuddeen na zaune afalon,   komawa kan sofa yayi ya zauna, inda ya matso kusa da Adda Rahama wanda kecin abinci,  dubansa Adda Rahama tayi tare da cewa. "Bafa zanci dakai ahaka ba, jeka wanko hannunka." Ɗan shagwaɓe fuska yayi tare da cewa. "Dan Allah Adda Rahama, muyi karɓe-karɓe, don nagaji, dama kafun na zauna ne kikace na wanko hannun nawa." Kai Adda Rahama ta girgiza tare da cewa. "Allah ya shiryeka, sarkin lalaci kawai, da ace kai mace ne, tabbas da anyi uwar son jiki." Murmushi kawai yayi tare da amsan spoon ɗin dake hannunta, haka suka shigayin karɓe-karɓe, idan tayi loma guda, ta bashi spoon ɗin shima yayi, duk wai saboda tsananin ganda, ɗauko spoon kaɗai ya gagaresa. Ummi ce tafito ɗaga cikin ɗaki, hannunta ɗauke da wayarta, duban Saifuddeen tayi tare da cewa. "Bappa Ali ne ya ƙira." Ɗago kai Adda Rahama tayi tare da cewa. "Akan maganan auren ne ko?." Kai Ummi ta jinjina tare da cewa. "Ƙwarai kuwa, koda na faɗa masa cewa, babu wacce ayanzu Saifuddeen ɗin keso, cewa yayi wannan ba uzuri bane, za'a ne mamasa ko acikin dangi." Idanu Saifuddeen yaɗan zaro waje, kasancewar yana kallon Ummin nasa, hakanne yasa ya fahimci me take faɗa. Murmushi Adda Rahama tayi, ɗan satan kallon Saifuddeen ɗin tayi, cikin kulawa tace. "Hakan ma yayi, tun da dai shi yace bashida zaɓi." Hayatuddeen ne ya ɗago kai tare da duban Ummi, cikin nutsuwa yace. "Acikin dangi kuma tab, nikam dai banso Hamma ya yi auren dangi, to idan ma hakane ae ga nan Amina da Asma'u, duk suna sonshi, musamman  ma Ameena, dake bala'in sonsa ae sai ya zaɓi ɗaya acikin su ko?." Ɗan jim Ummi tayi, nan kuma tasaki murmushi, cikin gamsuwa da kalaman Hayatuddeen tace. "Tabbas, ka ga kuwa ni na manta ma da batun Ameena, gaskiya yarinyar akwai hankali, sannan kuma tana da kirki sosai, don ko lokacin da yake jinya a Hospiatal ɗin Abuja, ta kula dashi sosai, gaskiya na yaba da hankalinta sosai tana son Babana." Duban Ummi Adda Rahama tayi tare da cewa. "Okay wannan nurse ɗin ba, gaskiya nima yarinyar ta kwanta min arai, sai-dai kuma wacece Asma'u, don ban shaida ta ba." Carab Hayatuddeen yayi inda yace. "Wata jarumar film ne, kinma santa ae, wannan Asma'u Ahmad Matawalle wanda take rawa da waƙa, tauraronta yana haskawa sosai." Idanu Adda Rahama ta ɗan zaro tare da cewa. "Mai rawa da waƙa kuma? chab awani gidan? gaskiya a'a, Ameenan dai tayi, don ƴar gidan mutumci ce da dukkan alama, kuma Saifuddeen da yawan kishi ai bazai iya aurenta ba." Cikin gamsuwa Ummi tace. "Tabbas nima Ameenan tafi kwanciya min arai, don dai ita Asma'un kam sam batayi ba, don idan ma muka zaɓeta bamusan da wanne ita kuma zata zo ba, duba da irin lalurar da yake fama da ita ma, sam baidace ya auri wata ƴar nanaye ba, wanda suka saba cuɗanya da maza, ko yaushe suna cakuɗe da maza awaje guda ga Saifudden da ɗan karen kishi, balallai ma yasamu ingantacciyar kulawa daga gareta ba, Ameena ɗin dai ita muka zaɓa." Nan Adda Rahama ta jinjina kai cikin gamsuwa. Shikuwa Saifuddeen daya duƙar da kanshi kasa, sai alokacin ya ɗago, kasancewar bai kallesu ba, hakan yasa baiji mai suka tattauna ba. Madanannin wheellchair ɗinsa ya danna, kai tsaye yanufi hanyar barin falon, don yagaji so yake yaɗan je ya kwanta ya huta. Yana fita Ummi ta dubi Hayatuddeen wanda keta aikin zubawa cikinsa abinci, cikin kulawa Ummi tace. "Hayatuddeen bani wayarka." Adaburce ya ɗago kansa, kasancewar yakai loman abinci bakinsa, hakanne ya sakashi ƙwarewa, take tari ya sarƙesa, da mamaki Ummi ke kallonsa, yayinda Adda Rahama kuma keyi masa sannu, botle water ta miƙo masa, nan ya amsa haɗe da kafa bakin goran abakinsa, saida yasha sosai kafun yaji ya samu relief,   cikin kulawa Ummi tace. "Sannu, haba kaima sai cikawa cikin ka abinci kake babu ko tsayawa, tayaya bazaka ƙware ba, bacin abincin ba guduwa zaiyi ba, kana abu kamar mara gsky." Shiru yayi tare da ƙoƙarin neman hanyar barin falon. Dubansa Ummi tayi tare da cewa. "Ina kuma zakaje? bacewa nayi kabani wayarka na ɗau number'n Ameena ba." Jin haka yasashi sauƙe gagarumar ajiyar zuciya,  zaro wayar daga cikin al'jihun wandonsa yayi, nan yashiga contact ɗinsa, inda ya laluɓo number'n Ameena'n, nan ya miƙawa Ummin nasa. Tsab Ummi ta kwafe number'n Ameena'n, inda ta sanya awayanta, kana ta miƙa masa wayarsa, haka ya wuce sama sumu-sumu, daganinsa kasan bashida wadataccen gaskiya. Nan Adda Rahama da Ummi suka ci gaba da tattaunawa akan sabon auren da za'a ƙarawa Saifuddeen ɗin, sai ayanzu ne suma suke ganin cancantar yin hakan, saboda Zaleeha ta gujesa, tana ganin cewar shi nakasashshe ne, yayinda su gani sukeyi dan shi nakasasshene yasa ta gujeshi sannan babu wata mace wanda zata iya zama dashi, hakan yasa dole ne ma su Aura masa Ameena, tun da dai ita tana son shi, sun tabbatar da cewa kuma zata kula dashi. Sun ɗan taɓa hira kafun Adda Rahama ta tafi, Ummi kuma ta nufi ɗaki ta kwanta, bayan taƙira Bappa Ali ta sanar masa zaɓin da tayiwa Saifuddeen ɗin, sosai shima Baffa Ali'n yayi na'am da batun, nan take yaƙirayi Baba Malam ya sanar masa, da batun,  sosai Baba Malam yaji daɗi, don kuwa ko ba komai hakan da sukayi sun karramasa. Saifuddeen kuwa yana shiga ɗakinsa, ya soma rage kayan jikinsa,  ƙarasawa gaban tankamemen bed ɗinsa yayi, nan ya sauƙa akan wheellchair ɗinsa, inda ya hau gadon. Lumshe idanunsa yayi tare da jawo blanket ya rufe jikinsa,   maganar ƙarin auren nasa daya dawo cikin kunnensa ne, ya sashi jin wani ɗaci a maƙoshinsa, sam shi baima ɗauki abun agaske ba, yasan suna faɗa ne kawai, amma shi ina yaga ta wani ƙara aure, shiru zaiyi ya ƙyalesu, yasan nan da kwana biyu suma zasu daina batun. Yana nan kwance, yaji vibration na wayarsa, don dama akusa dashi take. Kasancewarsa wanda bayajin magana, ko kuma wani sauti, hakan yasa koda yaushe wayarsa a vibrate take,  domin ta hakanne kaɗai zai gane cewar an turo masa saƙo, domin idan kunnensa baya ji, to ai jikinsa naji, don aduk sanda wayan ke kusa dashi, ko kuma take jikinsa, to zai jita tana rawa, hakan kuwa alamane na cewar an turo masa saƙo, ɗaukan wayar yayi tare da dubawa, ganin  saƙon na Ummin sane ya sashi buɗewa. Number'n wayane arubuce da kuma rubutu aƙasan sa kamar haka. "Wannan number'n itace number'n matar da na zaɓa maka amatsayin wacce zaka aura, saboda haka kayi saving ɗinta." Yana gama karanta saƙon ya tashi zaune cikin hanzari, jiyayi gabansa ya faɗi, cikin sauri ya jawo rigarsa wanda ya cire, nan ya sanya tare da hawa kan wheellchair ɗinsa, ahanzarce ya nufi part ɗin Ummi'n dan yafa lura su da gask suke nufin ƙara mishi auren. Koda yaƙarasa falon ta bai ganta ba, kai tsaye yanufi bedroom ɗinta. Tsayawa ajikin ƙofar yayi, tare dayi mata knocking,  Ummi dake kwance jin ana knocking yasa ta tashi ta zauna, murmushi tayi don tasan cikin biyu za'ai ɗaya, ko Saifuddeen ko kuwa Raleeya. "Shigo." Ta faɗa ataƙaice. Da sauri ya tura ƙofar ya shiga, Ummi na ganinsa taɗan tsume, tare da dubansa. Ƙarasowa yayi har gabanta, inda ya kamo duka hannayenta, kansa ya shiga girgiza mata, alaman "a'a." murmushi tayi tare da cewa. "A 'a me? bazakayi auren ba ko kuwa me? ko bakason zaɓin danayi maka, ba kuma zaka iya karɓanta matsayin zaɓina ba?." Shiru yayi tare da ɗan lumshe idanunsa, kansa ne ke sarawa, cikin body language ɗinsa, yace. "Bawai zaɓinki bane banaso Ummi, ni auren ne banaso, ki dubeni ki gani fa, tayaya zan iya rayuwa da mata biyu, ko kun manta abun da Dr. ya faɗa ne, ina ɗauke da nakasa banjin cewa, zan iya bawa mata biyu kulawan daya dace dasu ba." Dariya Ummi tasanya, tare da dubansa, saida tayi dariya sosai sannan taɗan soma tsagaitawa, shikuwa Saifuddeen kafeta yayi da idanunsa, tare da sanya mata fuskan tausayi. Ɗan tsagaitawa da dariyan Ummi tayi tare da cewa. "Ikon Allah, Yau kuma Saifuddeen kaida kanka kake ƙiran kanka da Nakasashshe? duk saboda ance ka ƙara aure shine har ka aminta cewar kai nakasashshe ne, har kuma ma kake ƙiran kanka da hakan, tsawon lokaci ban taɓa ji kaƙira kanka da wannan sunan ba, amma yau sai gashi da bakinka ka faɗa, ka kuma nanata.  hmmm lallai ma kuwa to wallahi in sha Allah auren nan babu fashi, sai anyi shi, na kuma gama yi maka zaɓi, umarni ne idan kuma kace a'a, shikenan saika ƙira surukin naka wanda ya yanke hukuncin, kace masa kai bazaka bi umarninsa ba." Idanunsa ya lumshe, jin zuciyarsa yake tayi masa nauyi, a kasalance, cikin yanayi marar daɗi yace da Ummi, ta sanar dashi, "Wacece zaɓin nata?." Nan Ummi tace. "Idan yana buƙatar sani, zai iya zuwa ya tambayi Adda Rahama, zata sanar dashi koma wacece." Jin haka yajuya yafita jiki a mace, yana mai saƙawa ransa to wacece ina take ina suka samota da zasu liƙa mishi ita, tuno babu in da zai samu amsoshin duk waɗanan-nan tambayoyin sai wurin Adda Rahma. Ae kuwa kaman jira yake cikin sauri ya juya ya fice daga cikin ɗakin. Kai tsaye ɓangarensa ya nufa, inda ya kimtsa kansa,  koda ya fito text message ya turawa Ahmad kan cewar yana son ganinsa. Kasancewar Ahmad ɗin na cikin gida, hakan yasa mintuna kaɗan sai gashi ya fito. Cikin body language Saifuddeen ɗin yace da Ahmad. "Ya kaishi gidan Adda Rahama." Sanin kwanan zancen yasa babu musu, Ahmad ya ɗauko musu mota, nan suka shiga, inda ya jasu zuwa gidan Adda Rahaman bayan sun biya jonapwd sun ɗauƙi ishaq wanda a zaton Saifuddeen ishaq zaibi bayanshi. Koda Adda Rahama ta gansu batayi mamaki ba, don tun kafun zuwansu Ummi ta ƙirata ta yi mata bayanin komai. Tray ɗin drinks masu sanyi ta dire agabansu, Ahmad ne ya ɗauki kwalin exotic ya miƙawa ishaq kana shima ya ɗauka inda yasoma kwankwaɗa, don shi fes yakejin ransa bashi da wata damuwa. Hakama ishaq da shi yafi kowa jin haushin Zaleeha, kuma Babanshi ya mishi bayanin son ƙarawa Saifuddeen aure da Baban Zaleeya ya shiryawa. Saifuddeen kuwa fuska ya marairaice, duban Adda Rahama yayi, tare da ɗaukan wayansa, cikin message ɗin Ummi ya shiga, nan ya nuna mata fuskar wayar, tare da yi mata alaman tambaya, kan cewa. "Wacece? Ina take?". Murmushi Adda Rahama tayi masa tare da cewa. "Miye abun tada hankalinka haka ne Saifuddeen? da ka nutsu ma don amaryar taka ba ɓoyayya bace awajenka kasanta." Cikin son ƙarin bayani ya zubawa Adda Rahama'n fararen idanunsa. Duban tsab Adda Rahama tayi masa, kana cikin nutsuwa tace. "Nasan kasan Ameena ae, wannan nurse ɗin da ta baka kulawa, lokacin da kake jinya a Abuja, kafun ku wuce India, to ita ce dai Ummi ta zaɓa maka, nima kuma nayi na'am don yarinyar akwai hankali, Masha Allah. Ka tuna har gida tazo itada Mamanta suka dubaka da jiki." Idanunsa ya zazzaro waje tare da jujjuya kai da ƙarfi sosai yashiga mamaki, lokaci ɗaya yaji kaman an watsa masa ruwan zafi, amamakance ya ɗan ƙanƙance idanunsa, cikin yanayin maganarsa wanda ya saba, wato body language yace. "Allah ya sauwaƙe ni dai na auri wannan Ameenan, mezanyi da ita bazawara ce fa!." Cikin tsananin mamaki Adda Rahama ta dubeshi,  kallonsa tayi da kyau tare da faɗin. "Kai Saifuddeen banda sharri bazawara kuma? wa ya faɗa maka cewar bazawara ce?". Murmushin gefen baki yayi, tare da jijjiga kansa, in a body language ɗinsa yace. "Impossible!, nine zan auri bazawara? chab hmmm Allah ma ya sauwaƙe, sam banason sauran wani wlh Allah ya kiyasheni suɗe ƙashin da wani ya rigani tsotsa." Baki Adda Rahama ta buɗe fuska cike da tarin mamaki sauƙe a jiyan zuciya tayi tare da cewa. "Wai nikam wayace dakai itaɗin bazawara ce?." A shagwaɓe ya rubutawa Addan nasa. "Ae basai an faɗa min ba, duk ckekken Namiji in dai ya nitsu idan mace bazawara ce zai gane ta ido, kuma nayi imani cewa Ameena bazawara ce, saboda haka ni dai bana sonta wlh bazan iyaba, ba kuma zan aure ta ba." Ahmad da Ishaq kam dariya sukeyi sosai fahimtar abinda yake faɗin. Baki Adda Rahama ta taɓe, inda ta gyara zamanta, dubansa tayi da kyau,ido cikin ido tace. "Naji koma dai bazawara ce, ita Ummi ta zaɓa maka a matsayin mata, sannan da kake ta maganar cewa, ita bazawara ce, kai ɗin dakake magana saurayi ne kai? inace kaima bazawarinne tunda dai kayi aure." Bakinsa ya turo gaba, a shagwaɓe ya narke fuska, cikin body language yace. "Wallahi ni banason Ameena, yarinyar da idanunta abuɗe suke, ta fa riga da tasan Namiji, sannan kuma har yanzu ni matashin saurayi ne, tayaya ma zan yarda na auri Ameena." Duban Adda Rahaman yayi tare da kamo hannunta, cikin yanayin daya saba musu alaman magana yace. "Kin sanni tun ina ƙaramin yarona ma ko ta yaya bana amfani da tsohon abu, hatta kaya idan ya kasance gwanjo ne bana sawa, sannan idan yakasance wani ya taɓa amfani da abu, bana kuma amfani da abun, a iyaka tsawon rayuwata nafison komai sabo, koda wajen zama ne nafison sabo, banason wanda wani ya taɓa amfani dashi, harta mota ko wayar hannu, ban taɓa sayan second ba, komai na nafison yakasance sabo, ko lokacin da nake makaranta, ko yaushe ni nake zuwa first a acikin aji, bana taɓa yarda nazo second akomai na, to me yasa yanzu zan yarda na auri mace second hand? sauran wani, wanda wani ya cakalkala ya bari, ragowar wani fa Adda tunda nake gidannane kawai nataɓa sayan abu second hand kuma kin san shima saida na sabunta mana shi, bazan iya auren sauran waniba kinfa san inada kishi." Kansa ya girgiza tare da cije laɓɓansa. Baki buɗe Adda Rahama ke kallonsa, sosai take mamakin ƙarfin hali irin na Saifuddeen ɗin. Shikuwa Ahmad da shaq dake gefe sai ƙyalƙyala dariya suke tayi, don sosai show ɗin na Saifuddeen keyi musu daɗi. Ajiyar zuciya Adda Rahama ta sauƙe tare da cewa. "Koma menene dai Ummi ta gama magana, kuma ta yanke hukunci, wanda mu dukan mu mun gamsu, ta kuma ce zata sanar wa Bappa Ali, don asamu ayi bikin cikin gajeren lokaci, kaman yanda Baba Malam ya buƙata, kai da za'ayi maka auren gata ma, miye na damun kanka, sadaki, kayan aure, komai da komai, duk fa Baban Zaleeha yace ya ɗauke ma, wannan kaɗai bai isa saka farinciki ba, auren huce haushi fa zaiyi maka." Jan kujeransa baya yayi, inda ya kwaɓe fuska, nan ya dubi Ahmad yace dashi. "Su tafi." kana ya ja hannun ishaq Shidai Ahmad dariya kawai yake, har hakan yaso ƙular da Saifuddeen. Haka dai suka dawo gida, bayan sun sauƙe ishaq ko amota Saifuddeen fuskar nan tasa aɗaure take tamau. Suna isowa gida, kai tsaye part ɗin Ummi ya sake komawa. Ganinsa yasa Ummi kafesa da ido, cikin sanya fuskar tausayi, yayiwa Ummi alaman cewa. "Shi bayason Ameena, saboda bazawara ce, sannan kuma shi tsoronta ma ya keji, gata da kallon tsiya, sai kace mayya, gaba ɗaya idanunta abuɗe suke." Dubansa Ummi tayi, tare dayin dariyar zuci batayi mamakin jin cewa Ameenan bazawara bace, saboda kafun isowarsu Adda Rahama ta kirata tasanar mata. gyara tsayuwa tayi tare da cewa. "Allah mai iko, yau kuma Saifuddeen  kai ne me tsoron mace? uhmm saboda bakason auren ta  shiyasa kake tsoronta ko?" Sake shagwaɓe fuska yayi, duk yanda yaso Ummi ta fahimce sa, ƙiyawa tayi, daga ƙarshe ma juyawa tayi ta koma cikin ɗaki. Ganin haka yasashi komawa part ɗinsa, ransa duk ba daɗi, wani haushin Ameenan nema duk ya cika masa zuciya, wannan rana haka dai yayi bacci zuciyarsa duk ba dadi. Washegari. Yana gamayin break fast ya shirya kansa, inda ya ɗauki Sule driver suka nufi gidan su Ishaq, don tun adaren jiya ya tsara cewa zai je yasamu Dirankaɗi da maganar, wato Baban Ishaq kenan." Koda yaje Ishaq ne yayi masa jagora zuwa falon mahaifin nasa,  bayan sun gaisane Saifuddeen yayi masa bayanin duk wani abun daya kawosa, ta hanyar yi masa rubutu a laptop ɗinsa. Koda Dirankaɗi ya karanta murmushi yayi tare da duban Saifuddeen ɗin. Cikin son basa ƙarfin guiwa yace. "Tayaya kake tunanin cewa, bazaka iya auran mata biyu ba? Kai jarumi ne Saifuddeen, saboda haka kada kasa wani damuwa aranka zaka iya." Nan fa Saifuddeen ya tubure masa kan cewar lallai shi bazai iya ba, ganin haka yasa Dirankaɗi ɗaukar wayarsa, inda ya ƙira Bappa Ali, shi kuma Ishaq dariyan Saifuddeen ɗin kawai yake. Gaba ɗaya abun da Saifuddeen ɗin ya faɗa, shi Dirankaɗi ya maidawa Bappa Ali, nan Bappa Ali yace da Dirankaɗi, ya faɗawa Saifuddeen ɗin, aure babu fashi, tunda Baba Malam da kansa ya yanke hukunci. Koda Dirankaɗi ya faɗawa Saifuddeen ɗin, take yace. "To Baba nifa banida kuɗin auren ma in da ba sadakanta iyayenta zasuyi ba". Nan Dirankaɗi da Ishaq suka saka dariya, dubansa Dirankaɗi yayi tare da cewa. "Ae dama ba kaine zaka sayi komai na auren ba, auren gata za'ayi maka ae." Haka duk yanda Saifuddeen yaso ya kaucewa auren, Dirankaɗi da Bappa Ali sunƙi basa dama, dama shi Baba Malam baisan wainar da ake toyawa ba. Dole haka Saifuddeen ya dawo gida, zuciyarsa cike da tunani kala-kala. Haka akayi ta kai ruwa rana da Saifuddeen inda yaketa cemusu wai aifa Dr yace bazai iya zama da mata biyuba, Ya Adnan kuma yace a a ba wani Dr daya faɗi hakan. Ɓangaren Baba Malam kuwa, tuni ya turawa Yaya Ahmad kuɗi, kan cewar ya bawa Aunty Lubna ta shiga cikin shoprite na Abuja, tayi musu sayayyan kayan lefe,  wanda za'aiwa Saifuddeen sabon aure dashi. Yaya Ahmad  ne yace da Baba Malam ya amshi kuɗinsa,  shi zai haɗa lefen da kansa,  nan Baba Malam yace "a'a so yake komai na auren yayi da guminsa, da kuma haƙƙinsa, don ya ƙudurta aransa cewa, auren huce haushi da kuma gata zai yiwa Saifuddeen ɗin." Can ɓangaren Zaleeha kuwa, rayuwarta mai sauƙi take gudanarwa acan garin na Numan, zuwa yanzu bata da wani abinci sai kayan fruits,  dangin su apples da kuma ayaba, goiba dabina sai su water meloon, acikin ƴan kwanki kaɗan ɗin, tuni abubuwa da yawa sun sau ya mata, zuwa yanzu abu biyu ne ke damunta, wato tana jin can ƙasan zuciyarta bata son gudowan da tayi tana kewan kowa hatta su Ummi tana kewansu, ji take kamar ta koma amman da zaran ta tuna ta koma ɗin sai taji kanta yana juyawa sai taji ta gigice lokaci ɗaya taji kamar an ɗaure mata zuciyarta. Sai kuma nata soyayyar mutumin da har yanzu takasa sake sanyashi acikin idanunta, sosai soyayyarsa ke ƙara ninkuwa acikin zuciyarta, dashi take kwana kana dashi kuma take tashi, yayi mata tsaye acikin rai. Yanzu ma zaune take akan katifarta, laptop ɗinta ne agabanta, inda ta saka earpiece akunnenta, wani series film take kallo acikin laptop ɗin nata, don tahakane take samun rage kewa, wayarta dake gefe ne ta soma ƙara alamar shigowar ƙira, sunan Balkeesu ne ke yawo akan screen ɗin wayar, saida ta kusa katsewa ta ɗauka tare da kara wayar akan kunnenta. Daga can ɓangaren Balkeesu tace. "Mutanen ƙauye." Baki Zaleeha ta taɓe tare da faɗin. "Ya akayi ne." Balkeesu kuwa dariyar dake cinta arai ta danne tare da faɗin. "Lafiya lau, ya kike kwana biyu ina ƙiran number ki baya tafiya." Ajiyar zuciya Zaleeha ta sauƙe, cikin halin rashin kulawa tace. "Maybe matsalan network ne." Dariya Balkeesu tayi inda cikin zuciyarta tace. "Ko kuma matsalan wuta ba." Afili kuwa cewa tayi. "Dama Rabeel ne yace nayi miki magana, yana ta ƙiran wayarki amma bakya ɗauka, sannan yayi miki text duk babu reply, meyasa bazaki ɗauki wayarsa ba, ko kin manta cewar abokin aikin ki ne?." Baki Zaleeha ta taɓe tare da cewa. "Tayaya kike tunanin zan ɗaga ƙiransa, halan ya manta cewar ina da aure ne? igiyoyin auren wani ne fa akaina, to me yasa zan ɓata lokacina nakuma ɗaukarwa kaina zunubi wajen magan, da Rabeel wanda kuma bai zama lalle dole sai munyi magana ba." Hararan wayar Balkeesu tayi, kamar Zaleehan na ganinta, taɓe baki tayi tare da faɗin. "Uhummm su aure manya, dama naƙira ne kawai don naji ykk, da kuma dalilin ƙin ɗaga wayar Rabeel da kikayi." Ɗan jim Zaleeha tayi tare da cewa. "Bani da wani dalili naƙin ɗaga wayarsa sai na darajar auren dake kaina, kuma ma koda zai ƙira sau 100 bazan ɗaga wayarsa ba, saboda ina da aure, kuma shi ba muharrami na bane babu yadda za'ayi nayi magana dashi ina matar aure." "Okay." Balkeesu ta faɗa ataƙaice tare da kashe ƙiran, ita so take taga rayuwar Zaleeha tazama lalatacciya ta yadda zata samu damar maye gurbinta a ma'aikarsu da kuma gidan Saifuddeen, amman ta kaicinta ɗaya Zaleeha nada riƙo da mutuncinta na ɗiyamace musulma tana kare budurcinta da lallaɓashi tamkar ranta ga ibada. Ita kuwa Zaleeha aje wayar tayi tare da maida hankalinta akan laptop ɗinta. Itan kuwa Balkeesu tana kashe wayan, ta saki dariyan mugunta, inda a fili tace. "Ko ahaka aka tsaya awasan nasamu kaɗan daga cikin abun danakeso tunda ko yanzu shirinki na mushaƙata ya dawo hannuna." Can ɓangaren su Baba Malam kuwa, gaba ɗaya sun fita daga sha'anin Zaleeha, ko zancenta ma Baba Malam baiso ayi masa. Maryam kuwa sosai take cikin damuwa, domin kullum da tunanin ƴan uwa da kuma mahaifiyarta take wuni, ganin yanda ta damu sosai ne, yasa Ya Ameenu ɗaukan ta ya kaita wajen Baba Malam, nan Baba Malam yayi mata kalamai irin na mahaifa masu kwantar da zuciya, tare da sa mata al'barka, hakan kuwa yasa zuciyarta ta saki, kaɗan daga cikin damuwarta ya kau. Rayuwar Mama a Ɓilliri kuwa abun yazo mata cikin wani irin yanayi, komai ba yayi mata daɗi, zaman takura kawai takeyi agarin nasu, yayinda Zahira kuwa kullum bata da wani aiki, sai ƙworafi da mita, kan cewar ita lallai saida Maman ta maida ita gida, ita kuwa Mama har yanzu gani take kamar Baba Malam ɗin zai sauƙo yace su dawo gidan, don tasawa kanta aƙidar cewa bazata taɓa ƙiransa ta basa haƙuri ba, har sai shida kansa ya gaji yace su dawo. To gatanan dai rayuwar batayi mata daɗi, abinci ma bata samun wanda takeso, gaba ɗaya komai yayi mata duhu, badon komai ba kuwa saidan tana rayuwa acikin mutanen da gabansu da kuma bayansu duk duhu ne, basa ɗauke da haske ko kaɗan, zaman Ɓillirin sam baya yi mata daɗi Babanta kuwa duk da kafurine yaga rashin kyauta warta, shiyasa ya tsananta mata yace gata ga ƙauyen ta zauna kuma damuna na dawowa noma zatayi, Zahiri kuwa ji take kamar a rami take gida ba wuta bare fanka ko AC ba Radio bare tv babu firij bare kayan more rayuwa babu gado bare lafiyayyan katifa babu ƙamshin komai sai warin burkutu, rayuwa dai ta masu tsamari gashi ita Zahira an katse mata karatu ta. Ruda kuwa Addan Mama daɗi hakan taji dan ko yanzu ta samu sun zama dai-dai da ƙanwar tata, itama ta wahalan dai. Bayan Kwana Uku, da turawa Ya Ahmad kuɗin lefe, Baba Malam da kansa ya kimtsa, inda ya tsara tafiyarsu Abuja, shi da Dirankaɗi, da kuma Bappa Ali, yayinda za suje nemawa Saifuddeen auren Ameena, Alhaji Naseer Maichanji shine mariƙi ga Ameena, wanda yake ɗan kasuwa ne sosai, hakan yasa mafi yawancin mutane sun sanshi, koda zasuyi tafiyar tasu ta yanzun da expriance ɗinsu zasu tafi, kasancewar Dirankaɗi yasan Alhaji Naseer wanda a binciken da Dr Adnan yayi akan Amina a wurin Dr Aliyu ne sukaji komai na Amina. ananne Dirankadi ya gane ɗiyar tsohon abokin kasuwancishi shiɗin, har ma number'n wayarsa yana dashi, domin sun sha haɗa busineess dashi Alhaji Naseer ɗin tun shekarun baya. To kuma bisa jagorancin Dirankadin zasuyi tafiyar da tuni sun sanarwa Alhaji Nasir Daddy kenan zuwan nasu. Ɓangaren Saifuddeen kuwa shi har yanzu ganin abun yake, kamar almara, musamman idan ya tuna da cewar. "Ameena ɗin bazawara ce." Sai yaji sam shi bazai iya mu'amala da ita ba. Ƙarfe 10 na safiya dai-dai jirgin da zai ɗaga zuwa Abuja, ya kwashi su Baba Malam da Bappa Ali. Inda suka tafi da niyar cewa bazasu dawo nan Gombe ba sai an tsaida lokaci da kuma ranan aure, don suna sa ran cewa. "Insha Allah Alhaji Naseer ɗin bazai hanasu ɗiyarsa ba." Sun isa garin Abuja lafiya, inda Ya Ahmad da kansa yaje ɗauko su a airport, nan fa dukansu suka shiga motar, kaitsaye unguwar Asokoro suka nufa, wanda anan gidan su Ameena yake. Yayinda duk abinda akeyi Amina bata da labari. Maigadi ne ya wangale musu gate ɗin gidan, nan cikin parking space ɗin gidan Ya Ahmad yayi parking, dai-dai lokacin wani ɗan Dattijon mutumi me cike da kamala, wanda yasha adonsa cikin manyan kaya, yafito daga cikin wata ƙofa, ganinsu da yayi yasa ya nufosu cikin sauri, fuskarsa ɗauke da fara'a ya miƙa musu hannu, nan suka shiga gaisawa cikin mutunta juna, kai tsaye yayi musu jagora zuwa ɓangarensa, wani babban falo ne mai kyau, inda anan yake tarban baƙinsa masu mahimmanci. Zama sukayi, tare da sake sabon gaisuwa. Duban Dirankaɗi Alhaji Naseer yayi tare da cewa. "Alhaji Ma'aruf ashe rai kan ga rai?." Murmushin manya Dirankaɗi yayi tare da cewa. "Ƙwarai kuwa Alhaji Naseer, gashi bayan lokaci mai tsawo da muka ɗauka gashi kuma mun sake haɗuwa." Shima Alhaji Naseer ɗin murmishi yayi tare da cewa. "Allah Mai iko, gashi kuwa harda Malam Bashir Sulaiman Dukku kuka zo, a gaskiya yau gidana yana ɗauke da manya manyan baƙi, masha Allah sannunku da zuwa." ya ƙarishe maganar yana miƙawa Baffa Ali hannu Dai dai lokacin masu aiki suka shigo, nan suka cika musu gaba da kayan ciye ciye harma da dangin su snacks. Drinks ɗin kaɗai suka ɗan taɓa, nan Baba Malam da kansa ya gyara zama, duban Alhaji Naseer yayi tare da cewa. "Nasan zakayi mamakin ganinmu, to amma ance wanda yake da buƙata shi yake zuwa, ko ba haka ba?." Nan dukansu suka jinjina kai, inda Alhaji Naseer yace. "Ƙwarai haka ne." Ajiyar zuciya Baba Malam ya sauƙe tare da cewa. "To kamar dai yanda ka ganmu dukan mu nan al'khairi ne ya kawo mu, dan kuwa munzo newa ɗan mu auren ɗiyar ka Ameena, muna fatan Allah yasa ba ai mata miji ba." Ajiyar zuciya Alhaji Naseer ya sauƙe, tare da ɗan numfasawa, cikin murna haɗi da farin cikin ganin manyan malamai sunzo neman haɗa zuriya dashi a hankali yace. "Masha Allah, Haƙiƙa naji daɗin wannan zancen naku ƙwarai, sannan kuma ba aiwa Ameena miji ba, saidai kuma bazan ɓoye muku ba, magana ta gaskiya banine mahaifin Ameena ba, nine dai mariƙinta, dani da mahaifinta kuwa uwa ɗaya uba ɗaya muke, sannan kuma magana ta biyu dai ita ce, Ameena ba budurwa bace, bazawara ce, don kuwa ta taɓa aure, ta auri ɗan wajena Amir, sai-dai kuma da yake Allah bai tsara zamansu tare ba, sati ɗaya kacal auren yayi Allah ya kawo ƙarshensa, sannan ahalin yanzu dai babu wani wanda ta tsayar mazaunin wanda zata aura." Ajiyar zuciya suka sauƙe su dukansu, cikin gamsuwa Baba Malam ya gyara zama, inda ya fuskanci Alhaji Naseer, cikin yanayin dattako yace. "Alhamdulillah, duk da kafun muzo bamusan da wannan magana ba, koda muka jita yanzu kuwa bazaisa mu fasa niya da kuma ƙudurin dake ranmu ba, saidai kuma muma zamu faɗa muku cewar ɗan mu na ɗauke da laluri, wanda idan akayi dubida ƙaddara ce wanda zata iya hawa kan kowa, sannan kuma duk cikinmun nan babu wanda baisan cewa, Lafiya da rashinta duk na Allah bane, sannan shike sawa bawa cuta, kuma shike yaye masa, sannan lalurar da ɗan mu kedashi, bai tauyesa daga zama cikakken ɗa namiji ba, domin yana da lafiyar da zai iya kusantar mace, sannan yana da wadatar da zai iya zama da mace, saboda haka muna fatan hakan bazaisa ku hanamu ƴarku ba, saboda shi aure nufi ne na Allah, matar mutum kuma ance kabarinsa." Bappa Ali ne ya gyara zama tare da soma yiwa Alhaji Naseer ƙarin bayani, dan gane da larurar Saifuddeen ɗin, bai ɓoye masa komai ba, ya fayyace masa komai yanda zai fahimta. Jinjina kai Alhaji Naseer yayi tare da cewa. "Nafahimce ku, ƙwarai kuma ai nakasa ba kasawa bace, kana nakasashshe zai iyayin abun da wani mai lafiyan ma bai iyawa, tabbas kuma idan na fahimta kune iyayen Saifuddeen ko?." Cikin Mamaki suka kalli juna, Dirankaɗi ne yace. "Ƙwarai kuwa, amma dama kasan Saifuddeen ɗinne?" Murmushi Alhaji Naseer yayi inda yace. "Ƙwarai kuwa, ai sanadiyar ita Ameenan nasanshi, don ita ta kula dashi lokacin da yayi jinya anan, sannan kuma koda suka koma india, danaje wani business ɗina naje har New Delhi na dubasa, gaskiya ni kaina na yarda da ƙwazon sa, don dagani matashi ne mai tsayayyar zuciya, tabbas wannan nakasa tasa bazata sa mu hanaku auren Ameena ba, sai-dai kuma kunsan cewa itaɗin bazawara ce, ba budurwa bace daza'ayi mata dole, saboda haka idan kunbani dama zan shiga ciki don na tambayo ra'ayi da kuma zaɓinta, sannan zan ƙira ɗan uwana awaya zan sanar dashi nasan bazaiƙi amincewa ba." Nan su Baba Malam sukaji daɗin hakan sosai, har saida murnarsu takasa ɓoyuwa, Nan dai Alhaji Naseer ya miƙe ya wuce cikin gida, inda yace su bashi mintina kaɗan. Acan cikin gida kuwa, koda yasamu Momma da maganar sosai tashiga mamaki, sai-dai kuma wani tunani daya faɗo ranta, hakan yasata sakin murmushi tare da cewa. "Masha Allah, ae kuwa nasan Ameena ba zata ƙi ba, bana ƙirawo maka ita yanzun nan saikaji ta bakinta." Nan Momma tawuce ɗakin Ameena, koda Momma ta shaidawa Ameena ƙiran da Daddyn nasu keyi mata, hakan taji gabanta yaɗan faɗi, hijab ta zura ajikinta sannan ta nufi falon. Durƙusawa tayi agaban Daddy'n nasu, cikin rusunawa tace. "Daddy gani." Dubanta Alhaji Naseer yayi cikin kulawa, yayi mata bayanin komai. Mamaki, haɗi da zallan farin ciki ne suka cika zuciyar Ameena, wannan shi ake ƙira da ƙarfin ikon Allah, haɗi da kuma falalar addu'a, tabbas ko kaɗan bata taɓa kawowa aranta cewa zata samu Saifuddeen anan kusa ba, tabbas takai kukanta wajen ubangiji gashi kuma ya amsa addu'arta, inda ya share hawayenta, alokacin da bata zata ba. "Ameena kinyi shiru." Maganan Daddyn ya katseta. Murmushi tayi, cikin sassanyar murya tace. "Idan dai har ka aminta da auren Daddy nima na amince, bani da wani zaɓi sai naka." Farin ciki da jin daɗi ne suka lulluɓe zuciyar Daddy, nan yashiga sanya mata al'barka, inda yace tatashi taje. Wayarsa ya zaro, inda ya ƙira Alhaji Sadam, wato Baban Ameena, koda Baban Ameenan ya ɗauka, nan Alhaji Naseer ya labarta masa komai, hakanan Alhaji Sadam yaji zuciyarsa ta aminta da batun, nan take yace ya amince, inda yace da ƙanin nasa yayi komai, ai Ameena ƴarsa ce. Nan fa Alhaji Naseer ya koma falon tarban baƙinsa, nan yasanar dasu Baba Malam Amincewar Ameena, da kuma mahaifinta, take suka cika da tsananin farinciki, sosai sukaji daɗi, ƙwarai kuma sun yaba da karamcin mutanen. Nan take suka tsaida magana, inda anan wurin a take Baba Malam yabada sadaki Naira dubu Hamsin, sannan ya kuma ce nan da kwana uku za a kawo kayan lefe, ananne Alhaji Naseer ya yanke musu lokacin biki, wato nan da sati biyu masu zuwa, domin kuwa dukansu ajiƙe suke da naira saboda haka babu wani amfanin jan bikin yayi nesa. Haka suka rabu cikin mutunta juna, kowa zuciyarsa fes. Ɓangaren Ameena kuwa tana shiga ɗaki, tsalle ta buga cikin matsanancin mamaki tace. "Ya Allah idan mafarki nake ka tasheni na farka ka kuma tabbatarmin dashi a zahiri. Wayyo Allah na wai dagaske Saifuddeen zai aureni? zan zama mata agaresa, wayyo Allah na!! Alhamdulillah." Sulalewa ƙasa tayi inda tayi sujjadan godiya ga Allah, cikin matsanancin jin daɗi tace. "Tabbas Allah Shi kaɗaine bashida wani abokin tarayya, sannan shike isar mana da komai namu." faɗawa kan gado tayi cikin matsanancin murma tayi hugging pillow. Nan fa tashiga birgima akan gado tana dariya, mai ɗauke da tsananin farinciki. Littafina na kuɗine ga mai buƙata ya min mgna ta wannan no ɗin 09097853276.      *By* *GARKUWAN FULANI* [9/9, 9:05 PM] +234 806 222 4030: Sbp egwl Ɓangaren su  Baba Malam kuwa, kai tsaye gidan Ya Ahmad suka koma, inda anan suka ɗan huce gajiyansu, zama sukayi suna maida batun karamci da kuma halin dattako irin na iyayen Ameena'n, tabbas sun shaida cewa suna da mutumci, kana kowani mutum zai so haɗa zuri'a dasu.                                       Da misalin ƙarfe 6 na yammaci jirgin da zai maidasu Gombe zai tashi, hakan yasa 5::40  pm  ababban filin airport na Nnamdi Azikwe International Airport Abuja.    Ƙarfe shida dai-dai kuwa jirginsu ya tashi, bayan Baba Malam ya ƙara jaddadawa Ya Ahmad, maganan haɗo lefe da wuri, nan Ya Ahmad yace. "Insha Allah zaisa Aunty Lubna ta haɗo lefen, nan bada jimawa ba."                                       Bakwai dai-dai jirgin da ya ɗaukosu daga Abuja zuwa Gombe, ya sauƙa acikin Gombe International Airport.              Ya Ameenu  da kuma Ahmad ne sukazo ɗaukarsu anan airport ɗin.                                          Motar Ya Ameenu Baba Malam ya shiga, inda Bappa Ali da Dirankadi kuwa suka shiga motar Ahmad, don sune zasu je suiwa Ummi bayanin duk abun da ya wakana.                            Haka suka rabu da juna cikin aminci da salama.            Tun daga yanayin yanda Ahmad yaga fuskokinsu ɗauke da annuri, hakan yasa shi fahimtar cewa lallai anyi nasara tafiya tayi kyau, sosai kuwa yaji sanyi azuciyarsa.                           Koda suka ƙarasa gidan, a falon na Ummi suka zauna, cikin nutsuwa kuwa Bappa Ali da Dirankadi sukaiwa Ummi bayanin komai, sosai Ummi ta cika da farin ciki haɗi da jin daɗi,  haka kuma lokacin da aka sanya auren yayi mata daɗi sosai, dama ba ta son aja lokacin, nan dai  tasa aka kawowa su Bappa Alin kayan ciye ciye,  nan suka ɗan taɓa, daga haka Dirankadi ya ƙirayi driver'nsa,  nan ya zo ya maidasa gida, shikuwa Bappa Ali anan zai kwana, kasancewar qdare yayi, idan yaso gobe da safe, Ahmad ko sule driver ɗaya daga cikinsu zai maidashi.                           Can ɓangaren Saifuddeen kuwa, ganin sun dage da gaske suke maganar auren yasa, wunin yau duk bai fito waje ba, anan ɓangarensa ya zauna, yayinda ya maida hankalinsa kan Laptop ɗinsa yana aiwatar da sabon aikin da shugaban DSS suka bashi. Koda ya dawo sallan Isha, kai tsaye part ɗinsa ya koma,  kasancewar yau din ana yanayin sanyi hakan yasa  shi kwanciya da wuri, luf yayi acikin lallausan bargonsa, inda ya ɓoye kansa acikin bargon, ajiyar zuciya ya sauƙe tare da lumshe idanunsa, tunaninta ne kwance acikin zuciyarsa, sau da yawa idan ya tuna da ƙiriniya da kuma rashin ji irinta na yarintarta dama yanzun da takega ta girma, yakan samu kansa da sakin murmushi.  Da haka bacci ya ɗaukesa. Washegari. Tun da ya dawo daga sallan asuba ya koma bacci, bashine  kuwa ya farka ba sai wajen ƙarfe 10:30 am.    Ahankali yazuro da ƙafafunsa ƙasa, tare da jawo wheellchair ɗinsa, wanda akullum take kusa dashi, sam baya bari tayi masa nisa, hawa samanta yayi, kai tsaye ya nufi toilet, koda ya shiga ruwan wanka mai ɗam ɗumi ya haɗawa kansa, cikin haɗaɗɗen jakuzzie, nan ya zuba turaren wanka mai daɗin ƙamshi acikin ruwan,  Luf ya kwanta acikin jakuzzien tare da ɗan lumshe idanunsa. Sama da mintuna 10 ya ɗauka ahaka, yayinda yakejin daɗin ruwan, kasancewar ruwan nada ɗan ɗumi, shiyasa yakejin daɗi yanayin, domin kuwa yanzu ana weather ne na sanyi hunturu.   Wanka yayi kana ya ya rufe jikinsa da wani fari ƙal ɗin towel,  haka ya nufi ƙofar fita daga cikin toilet ɗin, jikinsa ɗauke da danshin ruwa, yayinda kwantaccen sajen dake kan fuskarsa ya ƙara lafewa, saman kumatunsa. Kaitsaye gaban drawer ɗinsa ya nufa, inda ya zaro kayan da zaisa, wani ƙaramin towel ya ɗauka sannan ya shiga goge ruwan dake jikinsa, yana kammalawa, ya ɗauki handryer wanda  dashi yayi amfani wajen busar da tarin sumar dake kansa, cumb yasa inda yaƙara gyara lallausan sajensa, yayi kyau matuƙa, wani body lotion mai sauƙin ƙamshi ya shafa ajikinsa,  dogon wandon pencil jeans ya sanya, kana ya zura wata haɗaɗɗiyar riga, wanda take kaman na sanyi domin harda hulanta, kasancewar rigar nada kalan grey hakan yasa sosai tayi masa kyau, yayinda agaban rigar aka rubuta NIKE da manyan baƙaƙe,  wasu combat shoe wanda suma na company'n NIKE ɗin ne ya sanya aƙafafunsa, sosai shigar tayi masa kyau, saiya fito kaman irin shahararren jarumin ƙwallon ƙafa,  wani simple watch ya ɗaura akan tsintsiyar hannunsa,  kana ya feshe gaba ɗaya jikinsa da turare, take ɗakin ya gauraya da daddaɗan ƙamshin turarensa.      Wayoyinsa ƙiran iPhone da kuma Samsung ya ɗauka, kana ya zura su cikin ajihun dake jikin haɗaɗɗiyar rigar tasa. Daga part ɗinnasa kai tsaye barayin Ummi ya nufa. Tun kafun isowarsa falon nata, ƙamshin turarensa ya rigayesa isowa. Cikin nutsuwa ya ƙarasa shigowa cikin falon,   Hayatuddeen ne zaune akan dinning area, yayinda ya saka pepper meat soup agaba sai sha yake.  Ƙarasowa dinning area ɗin yayi, dubansa Hayatuddeen yayi cikin kulawa yace. "Barka da fitowa Hammana." Kai ya jinjinawa Hayatuddeen din bayan yasaki taƙaitaccen murmushi, dai-dai lokacin Ummi tafito daga ɗakinta, ganin Saifuddeen ɗin yasa ta sakin murmushi cikin kulawa tace. "Masha Allah ka fito kenan, yanzu fa nake cewa Hayatuddeen ya gama ya ƙiraka, kazo kayi break fast."  Ummi taƙare maganar tana mejan kujera wanda take facing na Saifuddeen ta zauna, duk dama shi always akan wheellchair ɗinsa yake zama.    Raliya ce tafito daga cikin kitchine, hannunta ɗauke da plate.  Ganin Hamman nata yasata sakin murmushi, cikin nutsuwa tace. "G/N Hamma."   Kansa ya jinjina mata alaman ya amsa, zagayowa ɓangaren da yake tayi, nan ta aje masa plate ɗin da ta fito dashi daga kitchine ɗin, wanda saman sa ke ɗauke da roasted fish, wanda yaji kayan haɗi, hadda lemon tsami.   murmushi Saifuddeen yayi tare da dubanta, hannu ya jinjina mata alaman "Thanks."  Itama murmushin tayi, don dama tayi hakanne don ta faranta masa, kasancewar tasan yanason roasted fish. Nan ta zauna, inda suka shiga cin breakfast ɗin cikin nutsuwa,  Ya lura dukaninsu suna cikin farinciki, musamman ma Umminsa, wanda duk bayan ƴan mintuna kaɗan take sakin murmushi, haka dai suka kammala break ɗin nasu, nan ya dawo cikin falon Ummin ya kwanta,  Hayatuddeen kuwa ɗaki ya koma, inda shima yayi shiga shigen irin ta hamman nasa, nan yafito riƙe da jakarsa ta makaranta, duban Ummi dake zaune afalon yayi, cikin sangarta haɗi da zallan shagwaɓa yace. "Ummi zan tafi school, 11:30 muke da lecture." Batare da Ummi ta ɗago kanta ba tace. "To Autana adawo lafiya." Jin haka yasashi ɓata fuska ashagwaɓe yace. "Ummi kuɗin hannuna fa ya ƙare." Murmushi Ummi tayi, don dama tasan kwanan zancen. Dubansa tayi tare da cewa. "Kullum sai an baka kuɗi Hayatuddeen sai kace ƙaramin yaro." Cikin tura baki yace. "Ni ban san ammafin buɗe min ac da Hamma Saifuddeen yayiba, ya tarkata komai ya riƙe ko Atm ɗin ban taɓa riƙewa koda na wuni ɗayaba, sai dai inyi ta ganin Arlet yanata shiga ba sauƙi, ina ganin miliyoyi amman bani da damar taɓasu." Dariya Ummi tayi hakama Saifuddeen, dan zancen autan nasu ya nuna burinshi na a bashi kuɗi ya fara lalata. Shi kuwa auta sake shagwaɓe mata yayi, wai adole sai ta bashi kuɗi, saikace ƙaramin yaro, nan Ahmad yashigo ya iske suna maganan, Ahmad ne ya ciro 5k daga cikin aljihunsa, inda ya bawa Hayatuddeen ɗin, nan Hayatuddeen yasaki murmushi sannan yasakai yafice daga cikin falon. Nan Ahmad ya zauna acikin falon suka shiga ɗan taɓa hira da Ummi, Saifuddeen kuwa, luf yayi tare da lumshe idanunsa, kamar wanda ke bacci. Abuja Nigeria. Kwana biyu kenan da zuwan su Baba Malam Abujan, yayinda yau Tsab Aunty Lubna da kuma wata ƙawarta, mai suna Samira suka shiga cikin shoprite, don haɗo kayan auren, ba laifi kaya masu kyau da kuma tsada suka sayo, duk da cewa ran Aunty Lubna baiso ƙara auren na Saifuddeen ba tanajin taya Zaleeha kishi, tana kuma tausayawa Zaleeha a gaba, to amma tasan cewa koma menene hakan shine dai-dai, don itama guduwan da Zaleehan tayi ya sosa mata zuciya. Akwatuna goma sha biyu suka saya, kana kuma suka cikasu da kaya, sannan kuma suka saya wasu uku daban wanda ciki aka sanya kayan uwa da na uba. Haka dai suka dawo gida bayan motarsu cike da kaya. Aranan kuwa Ya Ahmad ya ƙira Baba Malam, inda yasanar dashi cewa, anagama haɗa kayan auren. Kasancewar da dare ne Ya Ahmad da Baba Malam ɗin sukai waya, hakan yasa washe gari da safe, Baba Malam yaƙirayi Bappa Ali ya sanar masa, nan Bappa Ali yace. "Zai sanar da Ummin, sai susa ranan da za'a kai kayan." Hakan kuwa akayi don bayan sallan Azahar Ummi na zaune akan sallaya, sallame sallan ta kenan, wayarta tasoma ruri, ɗaga ƙiran tayi, bayan sun gaisa da Bappa Ali'n ne kuma, yake shaida mata cewar. "An kammala haɗa kayan auren, yanzun ita zata sanya ranan da za akai kayan." Cikin jindaɗi da gamsuwa Ummi tace. "Masha Allah, amma ni sai nake ga kamar ku ya kamata kutsai da ranan kai lefen, tunda dai auren bawani lokaci mai tsawo aka ɗauka masa ba, yanzu gashi kamar wasa har anci kwana uku acikin ranakun." Cike da gamsuwa Bappa Ali yace. "Tunda yau takasance asabar ne, to ranan litinin da safe, sai waƴanda zasu kai lefen su shirya." Nan Ummi take sanar dashi cewa. "Goggo dada, Adda Rahama, da kuma Ahmad, sai kuma Hayatuddeen, sune wanda zasuje, amma bawai kai tsaye abujan zasu nufa ba, a Kaduna gidan Raihana zasu sauƙa tukun." Nan dai tace ya kawo shawaransa. Cikin gamsuwa Bappa Ali yace mata. "Hakan ma yayi." Nan akayanke cewa, ranan litinin zasu kai lefen. Ummi na gama waya da Bappa Ali'n, numbern Adda Rahama ta ƙira, nan take shaida mata duk yanda sukayi da Bappan nasu, sosai itama Adda Rahama tayi na'am da hakan. Nan dai sukayi sallama. Numan. Zaman Zaleeha a numan ya miƙa sosai, duk da cewa bawai tanajin daɗin rayuwa acikin ƙauyen bane, amma babu laifi tana ɗan samun abun da take ɗan so, tunda da kuɗi a hannunta, rayuwa take cike da kaɗaici, saidai wani lokaci wayarta da kuma tsohuwar laptop ɗinta suke ɗebe mata kewa. Sai kuma wata sabuwar ƙawa wacce take ƴar fulani da tayi, inda sun haɗu ne, abakin kogi, don wani lokaci Zaleeha kan zuwa bakin kogin ta zauna, itakuwa sabuwar ƙawar Zaleehan mai suna Aisha, anan cikin wani ɗan ƙaramin rugar fulani dake kusa da Numan ɗin take, wanda yake rugace na zallan fulani sannan kuma dukansu musulmai ne, babu christan ko ɗaya acikinsu, tun Zaleeha bata sake da Aishan ba, har dai zuwa yanzu suka sama, domin kuwa taji daɗin haɗuwa da Aishan, kasancewar sosai Aishan ke ɗebe mata kewa, ta wani ɓangare kuwa mamaki take, kasancewar ansan cewa fulani suna aurar da ƴaƴansu da wuri, sai gashi ita kuma Aishan karatu ma take acikin birni, inda take aji biyu a university, wato level two, duka duka Aishan bazata ɗarawa Zaleehan ba, domin kusan ma kansu ɗaya, haka ma dai shekarunsu, sai-dai Zaleehan tafi Aishan cika dama duk wani abu na gogewa. Yanzu ma dai tsab ta gama shirinta, cikin wani riga da sket na material masu kyaun gaske, wani babban mayafi ta yafa ajikinta, wanda yazo har ƙasa ya ɓoye duk wani kyawun surarta, waya da kuma power bank ɗinta ta ɗauka, duban Aishan dake zaune tayi. Aishan ma dubanta tayi, ganin Zaleehan ta kammala shirinta yasa tace. "Masha Allah, kinga yanda kikayi kyau kuwa, sau dayawa ina mamakin ki, duk da cewa aƙauye kike zaune, amma kuma kullum ƙara kyau kike, yanayin shigarki ta kame kai tana matuƙar yi miki kyau." Murmushi Zaleeha tayi tare da cewa. "Uhumm kedai Aisha bakya gajiyawa da surutu, kullum ganin kyauna kike ke bakya ganin naki, dan Allah tashi muje, yau kam naƙosa muje gidanku, kodan ma na huta, da gorin da kikemin, kan cewa da kike, wai kullum ni bana zuwa gidanku, saidai ke kizo." Miƙewa Aisha tayi tana dariya, nan suka fito daga ɗakin. Babu kowa atsakar gidan, domin kuwa tun safe Elizabet, da kuma Solomon suka tafi church, kasancewar yau Lahadi. Suna fita Zaleeha ta jawo ƙofar gidan ta rufe, nan suka ɗauki hanya zuwa cikin rugar su Aisha, wanda yake nan kusa bashi da nisa, Koda suka shiga cikin rugar sosai Zaleeha taji zuciyarta tayi sanyi, sakamakon ganin yanda jama'ar rugar keta hada hadansu, wanda dukansu musulmai ne kana kuma fulani masu mutunci waɗanda hasken addini ya ratsasu, don da ka kallesu zakaga hasken musulunci agoshinsu, idanu ta lumshe, tare da sauƙe ajiyar zuciya, tabbas akullum tana ƙara godewa Allah daya yita musulma, domin kuwa tabbas duk wani addini da ba na musulunci ba, babu komai acikinsa sai ɓata, musulunci shi kaɗaine haske. Koda suka ƙarasa gidan nasu Aisha, cikin girmamawa ta gaishe da Innar na Aisha, haka dai suka ɗan gaggaisa da ɗan sauran jama'ar gidan. Nan suka zauna da Aisha'n, suka shiga ɗan taɓa hira. Sun ɗan jima suna hira ganin cewa la'asar ta kusa ne, yasa Zaleehan miƙewa, nan tace zata tafi, batason yammaci ya mata awaje, Inna Maman Aishan ne, ta bata pure nono cikin wani babban gora, wanda aka zuba zuma acikinsa, Aisha kuwa da kanta ta gasawa Zaleehan naman ƙatuwar Zabuwa, duk yanda Zaleeha taso kin amsa, saida suka sata ta amsa, nan tayi musu godiya sosai, sannan Aisha ta rakota, har kusan wajen rugar, daga haka sukai sallama, inda Aishan tace da Zaleeha sai tazo. Batayi wani tafiya mai nisa ba ta iso gida, nan ta iske har zuwa wannan lokacin su kawun nata basu dawo ba, ɗakinta ta shiga inda ta aje nama da kuma nonon da suka bata. Fitowa tayi donyin alwalan sallan la'asar, dai-dai nan Elizabet ta shigo cikin gidan, kamar an jefota ba sallama duk tayi wujiga-wujiga da ita, ƙafarnan tata tayi futu-futu, idanunta kuwa sunyi tsuru tsuru, alamun gajiya da wahala ya bayyana ƙarara ajikinta. Dubanta Zaleeha tayi, kana ta kau da kanta gefe, da taso yi mata sannu da dawowa, amma tunowa cewa Elizabet ɗin daga church take, hakan yasa ta fasa, zama tayi akan dakali, tare da jawo ƴar butar ta, ta soma al'wala. Elizabet kuwa kan wani benci dake tsakar gidan ta baje, nan tashiga maida numfashi akai-akai, saikace wacce tayi wasan tsere, amatuƙar gajiye ta ɗago kai ta dubi Zaleeha, wanda ke gudanar da al'wala cikin nutsuwa, ƙura mata idanu Elizabet ɗin tayi, tana me kallon yanda take alwala'n, cikin ranta tace. "Oo ni Elizabet kalli yanda suke gudanar da ibadansu cikin nutsuwa da kwanciyar hankali da jin daɗi, batare da wani hayaniya ba da ife-ife da raye-rayeba." Ajiyan zuciya ta sauƙe tare da ɗan gantsarewa dan azabar ciwon da ƙugunta yakeyi sabida wuni rawan da suka wuni tiƙawa a majami'ar bautar tasu. Duban ƙafanta wanda sukayi suntum tayi, hakan kuma ya farune sakamakon tiƙar rawa da tayi a church, don kuwa tun safe suke rawan bahutu, gaba ɗaya ta gaji. Idon dai ta zubawa Zaleeha tana ganin yadda take gudanar da harkar ibadarta a mutunce. Ita kuwa Zaleeha, tana alwalanne amma gaba ɗaya kewar da begen gida da danginta da Baba Malam ne ya cika zuciyarta, sosai takejin kewar mahaifin nata, tana matuƙar son Baban nata ƙwarai da gaske, tabbas ta wani ɓangare tanajin son komawa gida, tana so da ƙaunar taga tayiwa mahaifinta biyayya tana son farin cikin shi dana Ya Ahmad koda irin al'ƙawarurrukan da ya mata, tana jin ciwo a ranta ace da aure a kanta a kuma bata gidanta ɗakinta damahaifinta ya umarceta data zauna lokuta da dama tamkar tayi zama tsuntsuwa tayi fiffige ta koma cikin iyayenta tayiwa mahaifinta biyayya, koda ko sanadin rasa masoyin nata zaisa ta rasa ranta. To amma hakanan takeji kaman anɗaure ta da jijiyoyin jikinta, wanda takejin kamar dole akai mata zama anan Numan ɗin tanaji a ranta tana son ta koma amman duk sanda ta aiyana haka sai taji kamar a ɗaureta ne, a garin, haka dai ta kammala al'walanta kai tsaye ta wuce ɗakinta, a nan tabar Elizabet zaune tana ta faman maida ajiyar zuciya. Sallah tayi sannan ta jawo goran nonon, nan taɗansha kaɗan sosai kuwa taji daɗinsa, kasancewar bata wani jin yunwa yasa ta ajiye, kan cewar sai zuwa dare taci zabuwan da kuma nono'n.... Gombe State. Kasancewar yau ya kasance litinin, kuma yaune su Adda Rahama zasu wuce Kaduna, daga nan kuwa Abuja zasu inda zasu ɗau lefen agidan Ya Ahmad, sukai zuwa gidansu Ameena. Ƙarfe 9 dai-dai dukansu suka hallara afalon na Ummi, Adda Rahama, Goggo Dada, Ahmad da kuma Hayatuddeen, sune wanda zasu tafi, tun ƙarfe 8 Raliya ta gama musu break fast, inda sukaci suka ƙoshi, ƙarfe goma dai-dai jirgin dazai kwashesu zuwa Kaduna zai tashi, hakan yasa tuni suka kammala duk wani shirye-shiryensu, ɓangaren Saifuddeen kuwa, yana can part ɗinsa, baimasan wainar da suke toyawa ba. Kasan cewar lokacin ana tsaka da gyara Airport ɗin Abuja shine ya basu damar samun jirgin kaduna kai tsaye. Raliya da kuma Ummi sune sukai musu rakiya, har zuwa airport, kamar yanda yake arubuce kuwa ƙarfe 10 dai-dai jirgin nasu ya tashi. Kwata kwata tafiyar mintuna 46 jirgin nasu yayi, ya iso cikin airport ɗin garin Kaduna, koda suka sauƙo daga cikin jirgin nan suka iske Saminu najiransu, wanda shi da kansa yazo ɗaukarsu, sunyi farin ciki sosai da ganin juna, nan ya kwashesu cikin motarsa, suka nufi gidansa. Adda Rahama na shiga cikin gidan, Raihana ta rungumeta cikin tsananin farin ciki, itama Adda Rahaman rungume Raihanan tayi, don kuwa tayi kewarta, Hayatuddeen ne ya zumɓura baki tare da cewa. "Wayyo Adda Raihana ni bazaki rungumeni bane, kodai bakiyi kewata bane?." Dariya Raihana tayi tare dajan kumatunsa, cikin tsokana tace. "Ƙato dakai ne zan rungume ka, kaikam ai saidai ma nasa maka duka, kancewa ka shigomin gida, ƙato dakai, ai da katsaya daga waje." Dariya suka sanya su duka, Hayatuddeen kuwa, sake tunzura baki yayi, tare da faɗin. "Ae dama batun yauba nasan Raliya tafiki sona." Jin haka yasa Adda Raihana'n jawo hannunsa, cikin ƙaunar autan nasu, ta rungumesa, cikin son sanyaya masa zuciya tace. "Inasonka mana autan Ummi, ai kowa ya soka bayana ne, saboda kai fa yasa na shirya lafiyayyen girki, harma fa ferfesu nayi maka naka kai kaɗai na musamman." Jin haka yasa Hayatuddeen sakin murmushi mai ɗauke da tsananin farinciki. Cikin jin dadi yace. "Yesss shiyasa nake ƙara sonki Adda na, saboda koba komai kinfi su matar o'o kirki." Yaƙare maganar yana me satan kallon Ahmad. Dariya suka sanya don sarai sun gane dawa yake. Ahmad kuwa ƙwafa yayi inda yace. "Zamu koma ne yaro zakayi bayani agabanta." Nan dai suka zazzauna inda Raihana ta cika musu gabansu da kayan ciye ciye, haɗi dasu drinks. Saida sukaci abincin suka ƙoshi sannan, suka kimtsa don kama hanyar Abuja. Inda Ahmad ya ɗauki ɗayar motar Saminu, wanda ya ɗauki Goggo Dada da kuma Adda Rahama acikinsa, sai kuma Saminu wanda ya ɗauki, Hayatuddeen da kuma Matarsa Raihana. Kasancewar tsakanin Abuja da kuma Kaduna babu wani nisa, hakan yasa suka isa dai-dai an idar da sallan Azahar. Kaitsaye unguwar Wuse zone 2 suka nufa, wanda anan gidan Ya Ahmad yake. Koda suka ƙarasa gidan sun samu tarba me kyau daga wajen Aunty Lubna, sunkuwa ji daɗi ƙwarai, nan tafito musu da kayan auren suka gani, sosai suka yaba, don ƙwarai kayan sunyi kyau. Kimtsawa itama Aunty Lubna'n tayi, inda cikin motarta su Hayatuddeen suka loda akwatunan. Kaitsaye suka nufi Asokoro wato gidansu Ameena. Horn sukayi inda maigadi ya wangale musu gate ɗin gidan, suka shigar da motocinsu ciki. Tabbas gidan yayi kyau ba laifi, sannan suma masu kuɗi ne. Wata matashiyar Mata itace ta fito zuwa compound ɗin gidan, nan tayiwa su Adda Rahama jagora zuwa cikin gidan, yayinda driver da kuma mai bawa flowers ruwa sune suka shiga jidon akwatunan suna shigarwa zuwa falon gidan. Koda su Adda Rahama suka ƙarasa zuwa cikin gidan, sun samu tarba mai kyau, cikin karramawa matan da suka samu acikin falon suka tarbesu. Nan dai suka zauna inda suka gaggaisa. Take kuwa aka cika musu gaba da kayan shaye shaye. Bayan sun ɗan nutsane. Adda Rahama ta gabatar musu da kayan, nan suma suka yaba sosai, haka dai suka ɗan taɓa hira cikin mutunta juna. Koda suka tashi tafiya haka aka cika musu bayan motarsu da kayan ciye ciye. Nan dai suka rabu cike da ganin mutumcin juna. Duk wannan wainar da ake toyawa Ameena na kwance aɗaki tayi ƙumus, zuciyarta cike take da ɗanyar farinciki, ji take kaman tafi kowa sa'a aduniya, bazata iya misalta daɗin da takeji ba, tabbas babbar nasarace samun Saifuddeen amatsayin miji. Su Adda Rahama kuwa, gidan Aunty Lubna suka koma, nan dai suka ɗiba mata kayan ciye ciye dana shaye shayen da aka haɗosu dashi. Basuwani jima agidannata ba suka kamo hanyar Kaduna. Can gidan su Ameena kusa, ƙwarai sun yaba da kayan, kasancewar sanin Ameena ba budurwa bace, hakan yasa basui tunanin dangin Saifuddeen din zasuyi mata wannan karamcin ba. Koda Momma taƙirawo ta akan cewar tazo taga kayan, koda tagani taji daɗi ƙwarai, don harta farincikinta saida ya kasa ɓoyuwa, Allah kawai take ta godewa acikin ranta. Can Kaduna kuwa, gaba ɗayansu zaune suke afalon Raihanan, inda suke ta hiransu, Hayatuddeen ne yasaka bowl ɗin snacks agaba yanaci kana yana yagan cinyar kaza, sai wani jijjiga kansa yake, yana lashe red lips ɗinsa, wanda suke shige dana Hamma Saifuddeen ɗinsa. Dubansa Adda Rahama tayi, cikin zolaya tace. "Aikin ka kenan autan Ummi ci, acici kazar birni, niko da ace halittarka mai ƙiba ne, sannan ci nasa ƙiba, tabbas Hayatuddeen da yanzu girman jikinka ya cika falon nan." Idanunsa ya zazzaro waje. Cikin shagwaɓa yace. "Haba Adda saikace Yaya Saminu." Dundu Raihana takai masa tare da cewa. "Mijin nawa?." Dukansu suka sa dariya. Ahmad kuwa cewa yayi "Kaɗan ma kika gani indai Hayatuddeen ne." Shima dariyar yayi kana yace. "Ya Wareesu fa nake nufi." Haka dai sukaci gaba da hiransu, har aka ƙirayi sallan magriba. Saida sukayi sallan Isha kafun suka zauna inda suka sake kafa sabon hira. Haka dai sukaita hira har kusan goman dare, dagananne kowa ya nemi makwanci, Inda Ahmad da Hayatuddeen suka shiga cikin wani extra ɗakin dake cikin falon, Su Adda Rahama, da goggo Dada ma ɗaki guda aka basu. Domin kuwa gidan na Saminu akwai yalwatattun ɗakuna. Washegari da safe kuwa, Raihana lafiyayyen break fast ta shirya musu, inda suka cika cikinsu, nan kuma suka soma shirye-shiryen tafiya, don yau ɗinma jirgin ƙarfe 10 zasu bi zuwa Gombe. Saminu ne ya kaisu airport wanan karon hadda Raihana tayi musu rakiya. Basu bar airport ɗin ba kuwa saida suka ga tashin jirginsu, sannan suka dawo gida. Ƙarfe sha ɗayan rana acikin garin Gombe tayi musu, inda Sule driver yazo da babbar motar Saifuddeen har airport ya kwashesu zuwa gida. Afalon Ummi suka baje, wanda nan suka samu Saifuddeen zaune akan wheellchair dinsa, yana shan yogo fruit wanda Ummi ta haɗa masa, yayinda tasashi agaba sai tarairayarsa takeyi kamar wani ƙaramin yaro, shikuwa dama aikinsa ne shagwaɓa hakan yasa ya narke mata. Sam abun baya bawa su Adda Rahama mamaki, saboda sun san ƙaunar dake tsakanin Ummi da kuma Saifuddeen mai ƙarfi ce. Nan dai suka shiga labartawa Ummi, irin tarban mutumcin da suka samu daga wajen dangin Amina. Jin suna ta yaba kirkin dangin su Ameenan yasanya Saifuddeen kauda fuska, nan yamaida hankalinsa ga tv, don bama yason fahimtar mai suke faɗa. Anan dai Adda Rahama tayi sallan La'asar kafun Dr Adnan yazo ya ɗauketa. Goggo Dada ma ɗakin Ummi ta wuce don hutawa, shi kuwa Hayatuddeen sama ya haura, yana shiga ɗakinsa ya jawo wayarsa, data ya kunna sannan yashiga cikin Whatsapp ɗinsa. Nan ya iske saƙon Ameena. Inda tace. "Hey ƙanina." Ganin tana online yasashi sakin murmushi, nan yayi mata reply da cewa. "Sannu me wayo, wato kinma fara ƙirana da ƙaninki ko, saboda kinsan kinyi nasara, zaki auri handsome ɗin Hammana." Ameena dake kwance ganin saƙon Hayatuddeen din yasa ta saki murmushi, harda dariya. Cikin kulawa tace. "Dama na faɗa maka ae watarana insha Allah zan zama auntynka saboda haka biyayya dole." Koda Hayatuddeen yagama karanta saƙon dariya sosai yayi, nan dai ya tsaya suka ɗan taɓa hira da Ameenan, daga ƙarshe ganin ta sauƙa online, yasashi maida hankalinsa wajen chatting da abokansa. Yau kwana Uku kenan dakai lefen Ameena, har zuwa yau kuwa ko da sau ɗaya ne Saifuddeen bai taɓa tura mata saƙo ba, harkokin gabansa ma yake, yayinda ya watsar da batun auren acikin ransa. Inda yanzu auren ya kama saura kwana takwas kacal, domin dasa lokacin auren zuwa yanzu anci kwana shida acikin kwanakin bikin. Adda Rahama da kanta taƙirayi Ummi inda tace ta tambayi Saifuddeen, ko yayi mgna da Ameena'n, sai alokacinne ma Ummi ta farga. Aikuwa tana aje wayan, ta dubi Hayatuddeen dake kwance akan doguwar kujera yana chat. Cikin kulawa tace. "Hayatuddeen ƙiramin Hamma'n ka." Take kuwa ya miƙe, inda ya nufi part ɗin Hamman nashi. Koda yaje afalo ya iskesa, zaune akan wheellchair, inda yake sanye da dogon wando da kuma wata farar t shirt, laptop ɗinsa ne agabansa yana ta faman dannawa yana ta murmushin ganin amsar saƙon da ya kai kwana goma da turawa Zaleeha shi da numbarsa ta sirri in da ya nuna mata shi saurayine kuma yana sonta, to bata duba saƙonba sai shekaran jiya, bata kulashiba kuma sai yanzu da ya sake ce mata. "Hello my love". Koda ta buɗe saƙon sai yaga ta turo mishi amsa. "Wa iyazubillahi, kai wanne irin mutunne da zaka rasa wanda zaka so da bibiya sai matar aure, nayi block naka tun randa naga saƙonka sai kuma naga ka kuma min mgna ban san kai waye bane dake iya sarrafa na'urar da ba tasaba, na haɗaka da Allah da Manzonsa kada ka sake yimin mgna ni matar aurece, kaji tsoron Allah ka rabu dani!". Murmushi yaketayi yana mai-maita karanta saƙonta, yasan dole tayi mmkin cewar tayi blocking nashi kuma taga ya sake mata mgna. A ranshi yake cewa. "Baki san cewa nike sarrafa wayarki ba." Saƙon Ummin Hayatuddeen yasanar masa, sannan ya juya ya fita. Bai wani ɓata lokaci ba, ya nufi ɓangaren Ummin nasa bayan ya rufe system ɗin nashi. Tana nan zaune akan kujera, tana ganinsa taɗan sanja yanayin fuskarta, sarai tasanshi dayaga murmushi akan fuskartata, to tabbas tasan zai ɗauki maganar da zata faɗa masa amazaunin wasa kuma zai samu damar shigar da ƙorafinshi. Dubansa Ummin tayi bayan ya ƙaraso gabanta. Cikin kulawa tace. "Daga ranan dana baka number'n Ameena kawo yau sau nawa katura mata saƙo?." Gane abun da ta faɗa yasashi kwaɓe fuska, tabbas yasan dama watarana za'ayi haka. Ganin yanda ya kwaɓe fuska yasa Ummi cewa. "Au baka tura mata saƙon ba kenan?." Kansa ya jinjina alaman "Eh." danshi dama kwata-kwata bai iya ƙarya ba, sannan kuma koda wasa baya yiwa Umminsa ƙarya. Duban sa Ummi tayi tare da cewa. "To lallai katabbatar da yau katura mata saƙo, ko ka manta cewa aurenta zakayi ne?." Fuska ya sake kwaɓewa, tare da ɗan ciza kyawawan laɓɓansa, shikam yaga takansa da wannan liƙaƙƙen auren, hakanan an tilastashi auren wata mayyar yarinya, gashi tun ma bata shigo cikin gidan nasu ba, Umminsa ta fara takura masa akanta. "Kajini dae kam ko?." Ummi ta katse masa tunanin da yake. Kansa ya jinjina mata alaman yaji. Daga haka Ummi batace dashi komai ba, ta juya inda ta wuce ɗakinta, idanunsa yaɗan lumshe tare da buɗesu alokaci guda, kallonsa ya mayar ga Hayatuddeen wanda gaba ɗaya hankalinsa nakan wayarsa, sai murmushi yake yi, da'alama wani abun yake. Ƙura masa idanu yna ƴan wasu mintuna Saifuddeen yayi, kana ya girgiza kansa, cikin nutsuwa ya tura kekensa inda yabar falon. Bayan yadawo Sallan Isha ne, yaje part ɗin Ummin coffee ya amso tare da dawowa part ɗinsa, wayarsa ya ɗauka inda ya shiga cikin Whatsapp chat ɗinsa. Contact ɗinsa yabi inda ya laluɓo numbern Ameenan, da yayi seven ɗinta da sunan *Ta'annabi* a cewarsa wai sadaka za'a kawo misho ita shiyasa ya raɗa mata sunan Ta'annabi. ido ya ɗan zuwa no tata wanda hoton ta nema akan profile picture ɗinta. View ɗin hoton yayi, inda ya ƙurawa hoton ido. Sosai tayi kyau a hoton don tasha adone cikin wani jan lace, sannan fuskartan nan tayi fayau, don tana murmushi ne aka ɗauketa hoton, taɓe baki yayi tare da maganar zuci, mayya ko me ya tuno kuma sai yayi murmushi sannan ya rubuta mata saƙo kamar haka. "Slm". Ameena wanda kusan always tana online, kwance take akan gado, kamar da wasa kuwa taga numbern Saifuddeen ɗin yayi mata magana, azabure tatashi ta zauna, cikin zumuɗi tace. "Wayyo Allah ni daɗi kasheni, nakarɓi numbern ka wajen Hayatuddeen inason yi maka magana, sai gashi kai ka rigani." Cikin sauri ta amsa masa da. "Wslm". harma da ƙarin tambayarsa. "Ya gida." Yana karanta saƙon nata, yaƙara taɓe laɓɓansa, cikin zuciyarsa yace. "Su mazari, daga magana sai amsa babu ɗan jan aji kamar ba maceba." Ɗan jim yayi, cikin rashin sabo ya rubuta. "Ykk." Sannan ya tura mata. Lumshe idanu Ameena tayi tsabar daɗi, cikin mamaki tace. "Wai yau ni Ameena Saifuddeen ke tambaya ya nake?." Cikin sauri tayi typing.... "Lafiya ƙalau ya aiki, yasu Ummi?." Saida yayi kusan 3 minute bai buɗe saƙon ba, kafun daga bisani ya buɗe. Koda ya karanta ataƙaice yace. "Lfy." Ya amsa ataƙaice. Sanan ya kuma rubuta. "Meyasa kika amincewa Aurena, bayan kinsan da cewa, ni kurma ne, sannan kuma bana iya tafiya?." Ganin tambayar tasa yasa Ameena sakin murmushi, abayyane tace. "Kaiɗin nakeso Saifudeen ina matuƙar sonka, inasonka fiye ma da yanda nakeson komai." Arubuce kuwa cewa tayi. "Nakasa Ba Kasawa Bace, inasonka aduk yanda kake, sannan kuma zan zauna dakai ahaka, aurenka kuma ba kasawa bace." Koda ya karanta saƙon idanunsa ya lumshe tare dayin shiru, kamar zaice wani abu kuma, ataƙaice ya rubuta. "Okay saida safe jekiyi bacci." Daga haka ya kashe data'n sa, tare da aje wayan gaba ɗaya. Inda ya haurawa saman gado ya kwanta. A ranshi yake cewa. "Hmmmm kina dai da abin da kikeso a jikina, fitinanniya kawai mai idon cin maza." Ameena kuwa ganin ya sauƙa online yasa ta lumshe idanunta, daɗi da farin ciki su suka cika zuciyarta, haka tayita juyi akan gadon, wani irin shauƙinsa ne ke damunta, da haka tayi bacci. Tabbas akullum kwanaki ƙarewa suke, haka kuma lokaci na shuɗewa, akwana atashi asaran me rai, yau dai ya kama saura kwana uku kacal bikin Ameena da Saifuddeen. Inda daga ɓangare biyu na gidajen duk shirye shiryen bikin suke. Babu ma kamar gidansu Ameena, inda Ameena'n ke karɓan gyara na musamman, sosai ake mata gyaran jiki, hakan yasa fatarta tayi fresh. Ɓangaren gidansu Saifuddeen kuwa, su Ummi ne kaɗai ke kiɗa da rawansu, Saifuddeen iyakacinsa ido, tunkuwa ranan da yayiwa Ameenan magana ta Whatsapp baisake bi ta kanta ba. Zaune suke su dukansu Afalon Ummi, nan Ahmad ya shigo inda yake ƙara sanar dasu batun tashinsu don dama ya kammala gidansa tuntuni, Nan fa Saifuddeen ya kafe kan cewar Ahmad ɗin babu inda zaije, ae tunda ya saka baki ake ƙoƙarin yi masa auren dole dolensa kuwa ya zauna agidan. Duk kuwa yanda Ahmad yaso Saifuddeen da Ummi su barshi ya koma gidansa sun ƙiya. Nandai Saifuddeen yace Hayatuddeen ya dawo ƙasa, su kuma Ahmad ɗin su koma sama. Hakan kuwa akayi, inda aka gyara duka ɓangare biyun, Raliya ta tattaro kayanta suka dawo sama. Hayatuddeen kuwa ƙasa ya dawo. Can ɓangaren su Ahmad ɗin kuwa aka gyarawa Amarya Ameena. Sannu-sannu bata hana zuwa saide adaɗe ba'a je ba. Rana kuwa bata ƙarya. Yau yakasance Alhamis, inda gobe Jumma'a ɗaurin auren Saifuddeen da Ameena. Acan Abuja yau Ameena ta gudanar da walima, inda aka yi wa'azi mai ratsa jiki, sosai kuwa waliman ya ƙawatar, don Ahmad dakansa ya tura mata kuɗi a account ɗinta, inda yace tayi duk wani hidima da takeso. Kana kuma yaune akaiwa Amarya jere, domin kuwa Babanta da kansa yayiwa kamfanin masu saida furnitures magana, ta online suka sai kayan, wanda Ameenan da kanta ta zaɓi kalan da takeso. Ma'aikatan kamfanin kuwa suda kansu suka zo har gidan su Saifuddeen ɗin suka jera mata kayanta, sosai kuma yayi kyau. Washegari. Jumma'a. Ranan yau takasance jumma'a, wanda kuma ayau ɗinne za'a ɗaura Auren Saifuddeen da kuma Ameena. Tun safe kuwa Saifuddeen yaƙi fitowa, inda ya ce bashi da lafiya, sanin cewa Ameenan ba budurwa bace, kana kuma ba agari za'ai ɗaurin auren ba, yasa sam su Bappa Ali basu matsa masa ba. Ƙarfe tara dai-dai jirginsu zai tashi. Baba Malam, Bappa Ali, Dirankadi, Malam Adam, Baba Bello, Ishaq, Ahmad, Wareesu, Saleesu, Hayatuddeen, sune waƴanda zasuje ɗaurin auren, sai kuma Adda Rahama da Aunty Meena, wanda sune zasu ɗauko amarya. Ƙarfe tara acikin jirgi tayi musu, inda suka ɗaga zuwa garin na Abuja. Sun isa Abuja ƙarfe goma dai-dai, inda kuma za'a ɗaura auren ƙarfe 11 na rana dai-dai. Ya Ahmad ne yazo ɗaukansu kai tsaye Asokoro gidansu Amarya suka nufa. Nan suka tarar da ƙofar gidan ɗinke da jama'a, ƴan ɗaurin aure. Alhaji Naseer da kuma mahaifin Ameena Alhaji Sadam su suka tarbesu cikin mutum tawa, inda su Adda Rahama kuwa suka wuce cikin gidan. Kamar yanda aka sanya lokaci, ƙarfe sha ɗaya dai-dai jama'an dake wajen suka shaida ɗaurin auren Saifuddeen da Ameena, akan sadaki naira dubu hamsin. Nan fa jama'a suka dinga sanya alkahiri, da nema musu zaman lafiya. Acan cikin gida kuwa, amarya Ameena tayi kyau don an tsantsara mata meckup dai-dai misali, inda ta suturce jikinta da shiga ta al'farma, balaifi tayi kyau don kuwa sam bata da muni, saidai kuma bata da azababben kyau. Jirgin ƙarfe ɗaya zasu biyo don dawowa Gombe, hakan yasa Dady wato Alhaji Naseer da kuma mahaifinta suka jata gefe inda sukayi mata nasiha sosai mai ratsa jiki. Harma da ɗan guntun ƙwallanta. Daga haka su Adda Rahama suka kamata, inda aka sanyata a mota, ƴan uwanta biyu ne zasuyi mata rakiya. Akwai auntynta wanda ake ƙira da Aunty Zubaida, sai kuma ƙanwar mamanta, Aunty Zainab, nan dai suka ɗunguma dukansu zuwa airport. Ƙarfe ɗaya kuwa dai-dai jirginsu ya tashi, zuciyar Ameena cike da kewar gida. Sun iso cikin garin Gombe lafiya, inda lafiyayyun motoci har guda shida suka zo ɗaukarsu, Baba Malam dai kaitsaye gidansa aka wuce dashi shida Malam Adam, sai kuma Dirankadi da Ishaq, wanda suma kaitsaye gida suka wuce. Koda suka ƙaraso, sosai ƴan uwan Ameenan suka yaba da kyaun gidan nasu Saifuddeen, nan dai kaitsaye part ɗin Ummi aka wuce da ita. Tarba mai kyau Ummi tayi musu, tare da nuna musu ƙauna, haka ta jawo Ameenan jikinta cikin kulawa tayi musu addu'an samun zaman lafiya, da kuma zuri'a ta gari. Daga nan kuma Adda Rahama tayi musu jagora zuwa ɓangaren Ameenan. Nan ma sun yaba da tsaruwan part ɗin nata. Kasancewar waƴanda sukai mata rakiyan ba kwana zasuyi ba, ƙarfe 5 na yammaci dai-dai sukabi jirgi inda suka koma Abuja. Nan fa akabar Amarya Ameena ita kaɗai aɗakinta. Yayinda ƴan tsirarun mutanen da sukazo bikin, tuni suma sun koma, domin dama Ummi batayi wani gayya ba, Aunty Mina ma tabi Bappa Ali sun koma dukku. Haka gidan ya rage, daga Ummi, Adda Rahama, sai Raliya da kuma Hayatuddeen. Shikuwa Saifuddeen tuni dama yana ƙule acikin ɗakinsa. Koda akayi sallan Isha kuwa, saiga su Ahmad da Ishaq wai sunzo yi masa rakiya zuwa ɗakin amarya, abun ma dariya ya basa, nan dai ya haɗe gabar da yamma, inda yace. "Baya buƙatar rakiyan nasu." Duk yanda sukaso rakasa wajen Amaryar ƙiyawa yayi. Haka suka tafi suna masa dariya. Part ɗin Ummi ya nufa inda yasamesu zaune su dukansu afalo. Cikin salon shagwaɓansa, ya dubi Ummin, gane abun dayake nufi yasa tace da Raliya ta ɗauko masa flask ɗin coffe ɗinsa, don dama tuni ta haɗa masa. Yana amsa kuwa ya juya inda ya nufi part ɗinsa. Ta ɓangaren Zaleeha yabi inda yashiga falonsa, kai tsaye ɗaki ya wuce, kayan jikinsa yaɗan rage sannan yasha coffee ɗin, kan gadonsa ya haye tare da rufawa kansa blanket, sam babuma maganar zuwa wajen Ameena acikin ransa, don kuwa ko Zaleeha dayake mutuwar so, ranan farko baije ɗakinta ba balle wata Ameena da yasan jira take ta ganshi ta mishi fyaɗe dan ya dai san abinda take so. Can ɓangare Ameena kuwa koda tayi sallan isha, komawa tayi ta zauna jigum, kaɗaici ne ya dameta, tun tana zaune harta gaji ta kwanta, take kuwa bacci ya ɗauketa. Washegari. Tunda ya fita sallan asuba bai dawo gidan ba, can ya zauna amasallaci inda ya shiga rera karatun alƙur'ani. Ameena kuwa tana idar da sallah, ɗakinta ta kimtsa, sannan ta zura doguwar hijabinta ta fito. Nanne ta shiga ƙarewa ɓangaren nata kallo. Ganin wata ƙofa acikin falon nata yasata buɗewa, nan ta tsinci kanta cikin wani haɗaɗɗen falo wanda haɗuwarsa ya zarce misali, ƙamshinsa kaɗai da taji yasa ta fahimci cewa ɗakinsa ne. Ƙarewa falon kallo tayi sosai, sannan aɗaɗare ta nufi wata ƙofa dake cikin falon, wanda tana kyautata zaton cewa bedroom ne. Aɗan ɗaɗare tayo knocking, amma shiru ba'a amsa mata ba, tunowa da tayi cewar bazai jita ba koda yana ciki hakan yasa tatura ƙofar ahankali tare da tura kanta ciki, ni'imtaccen ƙamshin daya daki hancinta ne yasata lumshe ido, ƙara kutsawa cikin ɗakin tayi, baki ta buɗe tana ƙarewa aljannar duniyar ɗakinnasa kallo, komai dake cikin ɗakin ya haɗu, ganin baya cikin ɗakinne yasa taɗan sauƙe ajiyar zuciya. Komai dake cikin ɗakin nead, kan gadonne kawai dayake aɗan hargitse, cikin nutsuwa ta shiga kimtsa masa gadon nasa, sabon bedsheet ta shumfuɗa masa, kana ta sake share ɗakin. Nan ta fesa air freshner'n da ta gani asaman mirror'n ɗakin. Take ɗakin yasake ɗaukan ƙamshi. Fita tayi daga ɗakin inda kaitsaye ta wuce ɓangaren Ummi don ta gaida ita. Tana shiga kuwa ta samu Ummin afalo. Cikin ladabi ta rusuna har ƙasa tagaishe da Ummin, cikin jindaɗi haɗi da ƙaunarta Ummi ta amsa mata, tare da tambayanta ya kwanan baƙunta. Cikin al'kunya tace. "Alhamdulillah." Dai-dai lokacin kuwa saiga Saifuddeen din yashigo wanda dawowansa daga masallaci kenan. Afakaice Ameena tasaci kallonsa, shikuwa bai kalli inda take bama saima gaishe da Ummi da yayi. Fuska ɗauke da murmushi Ummin ta amsa. Cikin matsanancin nuna girmamawa Ameena. Tayi ƙasa da murya aladafce tace dashi. "Ina, kwana!." Muskarshi ya ɗan yamutsa tare da taɓe fuska, a hankali ya ɗan ɗago ida nunshi ya kalli fuskarta, kauda kanshi yayi dasauri kana ya...! By *GARKUWAR FULANI* [9/9, 9:05 PM] +234 806 222 4030:         Sbpett Lumshe idanunta tayi tana mejin wani irin sanyi na shiga jikinta, cikin wani irin tsantsar farin ciki ta samu kanta, hakanan takejin zuciyarta fes, gaba ɗaya duk wani damuwarta ta kau,  sake shigewa cikin blanket tayi,  cikin zuciyarta tace.   "Tabbas shiɗin na dabanne, duk da cewa namiji ɗaya na taɓa sani kafun shi, amma  nasan cewa, samun irinsa abune me matuƙar wahala."   murmushi tayi tare da ɗan cije laɓɓanta, cikin zuciyarta ta kuma cewa. "Wai ahakan ma don bashi da lafiya, duk lokacin da yasamu lafiya yaya kenan, tabbas ranar zai zautar dani zai sani duniya gajumare."  hannu tasa ta ɗan rufe fuskarta, sakamakon wani irin kunya da taji ya rufeta.     Can  cikin toilet kuwa Saifuddeen ne kwance cikin bathtube ɗin wanka,  yayinda kansa ne kaɗai ke waje,  ya lumshe kyawawan idanunsa, masu matuƙar kyau, ahankali yake fitar da numfashi,  wani irin sanyi haɗi da zazzaɓi zazzaɓi yakeji,  cikin yanayin dauriya haka yayi wanka, wheelchair dinsa ya jawo, kana ya hau kai, ƙarasawa gaban wani ɗan glass, dake kamar sip yayi, nan ya zaro ɗaya daga cikin bathrobe's ɗin dake cikin glass ɗin, sanyawa yayi ajikinsa, yayinda ya riƙe towel ɗaya ahannunsa yana goge jiƙaƙƙen gashin kansa, madannin wheelchair ɗinsa ya danna, tare da nufan hanyar fita daga bathroom ɗin. Ahankali ya buɗe ƙofar ya fito.        Cikin nutsuwa ya tura kekansa zuwa  gaban mirror, handryer ya jona tare da busar da gashin kansa,  turarensa mai sanyin ƙamshi ya fesa, nan ya ƙarasa gaban drawer'nsa, dogon wando da t shirt ya zaro, tare da sanyawa ajikinsa.   Nan ya nufi gadon nasa. Wanda har yanzu Ameena ke kananna ɗe akai.    Hannunsa yakai inda yaɗan janye bargon da take rufa dashi, kasancewar duk abun dayakeyi tana jinsa ba bacci take ba, hakan yasa   ta ɗago da kanta ta kalleshi.     Ganin cewa ba bacci take ba, yasashi jan kekensa baya,  yasake komawa gaban dressing mirror.        Ganin ya juya mata baya, yasa ta tashi daga kwancen da take.  Rigarta dake yashe bisa kan gadon ta ɗauka, nan ta sanya, ahankali ta sauƙo daga kan gadon, cikin yanayin sanyi ta wuce bathroom.          Dukkan abun da take yana lure da ita, dan yana ganinta ta gefen idonsa.      Ganin ta shige bathroom ne yasa shi, ƙarasawa jikin gadon, hannunsa yakai inda ya yaye bedsheet ɗin dake shumfuɗe akan gadon, cikin wani durtsbin wanda yake aje, ƴan kayayyakin da ba a wanke ba,  ya jefasa, sannan ya ciro wani sabo acikin drawer ya shumfuɗa, kasancewar sa mutum me tsananin son tsabta,  shiyasa baijin zai iya kwana akan  wannan bedsheet ɗin, domin idanunsa sun gane  masa sperm ya zuba kaɗan ajikin zanin gadon.              Yana gama shumfuɗa zanin gadon, ya sauƙa daga kan wheelchair ɗinsa, hawa kan gadon yayi  tare da jawo sabon blanket ya rufa ajikinsa.                    Kwanciya yayi tare dayin lub, sannu ahankali  yakejin zazzaɓin jikinsa na ƙaruwa.              Can cikin toilet kuwa  wanka Ameena tayi, sannan ta ɗauro alwala,  itama ɗaya daga cikin bathrobe ɗin nasa ta sanya,  nan ta fito daga toilet ɗin tana me goge kanta.         Handryer'n da yayi amfani wajen busar da gashin kansa, itama dashi tayi amfani, wajen busar da gashin kanta, daba yawane dashi ba, saidai yana da ɗan cika, amma baida wani tsawo. Dubanta takai garesa, ganin ya naɗe akan gado  tare da ɓoye jikinsa cikin blanket, yasa tayi tunanin cewa ko bacci ne ya ɗaukesa.     Ganin cewa bata da kaya anan ɗakin nasa, yasa cikin nutsuwa ta buɗe kofar ɗakin  ta fice.    Kaitsaye ɗakinta ta wuce. Nan ta sanya wata ƴar doguwar riga marar nauyi ajikinta,  turare ta fesa sannan  ta koma zuwa ɗakin sa, don ayanzu batajin zata iya kwana awani ɗakin bayan nasa, koda ta kwana anata ɗakin ma, tasan cewa bazata ji daɗin kwanciyar ba, kasancewar ta fahimci cewa, bacci yafi mata daɗi idan tana shaƙan daddaɗan ƙamshinsa. Koda ta koma ɗakin nasa, hayewa saman faffaɗan gadon tayi  tare da jawo sabon blanket ɗin ta rufe jikinta, kanta ta ɗaura akan pillow tare da lumshe idanunta.                 Jin alaman kwanciyarta ya sashi buɗe idanunsa, don dama ba bacci yake ba.                 Ɗan mirginowa yayi tare da juyowa, ya zama  suna fuskantar juna,  matso da jikinsa yayi kaɗan,  tare da sa hannunsa ya tallafi fuskarta,  hakanne yasa  ta buɗe idanunta.         Bakinsa ya ɗaura a dai-dai goshinta, inda ya ɗan manna mata sasanyan kiss.     Sosai taji abun ajikinta hakan yasa ta lumshe idanunta. A hankali yasa tafin hannunshi ya shafi fuskata, Jawota yayi ya mannata da jikinshi, cikin yanayin zazzaɓi da yakeji ya ruggimeta. sannan yasake rufasu da blanket,  shigawa cikin jikinshi tayi da kyau tare da lafewa tana sauƙe ajiyan zuciya, shi kuwa Saifuddeen bisa goshinta ya kuma sumbata kana ya rufesu da kyau saboda wani irin sanyi da yake ji.                 Itakuwa Ameena sosai ɗan kiss ɗin da ruggumar   da yayi mata ya jefata cikin shock, taji daɗi ƙwarai, dan kuwa koda wasa bata tsammaci kulawa daga garesa ba,  rungumeshi tayi tana murmushi.                 Shikuwa Saifuddeen yayi  hakanne, saboda yaga dacewar abun, bai kyautuwa ace yana shareta, sannan  kuma ya hanata kulawarsa, tabbas akwai haƙƙinta akansa, wanda kuwa idan bai sauƙe ba, Allah zai iya kamashi,  saboda haka dole zaiyi ƙoƙari sauƙe duk haƙƙinta daya rataya kanshi, amma badon wai yana jin sonta aransa ba sam babu ko ɗaya, ƙauna dai guda ɗaya ce, kuma tun a haɗuwar farko ya mallakawa Zaleeha gaba ɗaya ƙauna da zuciyarsa, saboda haka baijin cewa Ameena zata taɓa samun gurbi cikin zuciyarsa, saidai yayi mata kara da kawaici kawai dan darajar sonshi da takeyi tafi ƙarfin wulaƙantawa, amma bawai don yana sonta ba. Tana rungume dashi haka bacci ya ɗauketa,  shikuwa yajima sosai kafun bacci ya ɗaukesa,  saboda zazzaɓin jikin nasa yaƙi sauƙa.                           Ƙiran sallan asuban fari da akayi yayi dai-dai da lokacin dayi juyi, saboda gaba ɗaya zazzaɓi ya hanashi samun isashshen bacci,   ahankali ya tashi zaune,  hannunsa ya ɗaura akan wuyansa, sosai jikin nasa yayi zafi jau.   Cikin ɗan dauriya ya jawo wheelchair ɗinsa,   hawa yayi tare da shagwaɓe fuska, sam shi hakanan yake baida dauriyan ciwo, musamman ga  irin waƴannan ƙananun ciwukan, yafiso idan baida lafiya yayita zuba sakalci, haɗi da shagwaɓa tamkar ƙaramin yaro kuma ma dai halittarsa ce raki in yaji ciwo kaɗan zaitawa Ummyn shi da Adda Rahma Raki.       Bathroom yashiga inda ya ɗauro alwala, koda ya fito sallaya ya shumfuɗa, sauƙa yayi daga kan wheelchair ɗin, inda ya zauna akan sallayan.              Nafila raka'a biyu yayi,  yana idarwa ya jingina jikinsa da jikin wheelchair ɗinsa, wanda ke bayansa,  ganin alamun anshiga sallan asuba ne, yasa shi ta da nasa sallan a gida, dan sam baijin cewa zai iya zuwa masallaci, bama yajin ƙarfi ajikinsa.     Yana cikin gabatar da sallan Ameena tatashi, tasha mamakin ganinsa, dan kuwa tasan baya sallah agida,  nan dai ta wuce toilet ta ɗauro alwala, can gefe ta shumfuɗa sallayanta sannan ta tada nata sallan.              Saifuddeen kuwa yana idarwa, addu'a kawai ya shafa,  ataƙaice yayi azkar tare da ɗan jan jikinsa ya sake hayewa saman gado,  dan zazzaɓin ƙara hawa jikinsa yake, ko ina na jikinsa ya ɗau zafi jau, kamar wanda ake hura masa wuta, sake  duƙunƙunewa yayi acikin blanket, lokaci ɗaya ya fara masassara.               Koda Ameena ta idar da salla, cikin sanyi ta dubeshi,   tashi daga kan sallayan tayi nan taƙaraso zuwa jikin gadon.       Cikin kulawa tasanya hannu inda taɗan taɓa forehead ɗinsa, jin jikinsa da zafi yasa taɗan waro idanunta waje.     Cikin yanayin tausayinsa tace.    "Sannu baka da lafiya ne?"                        Idanunsa ya lumshe batare daya amsa mata ba, saboda sam baya son damuwa, cikin zuciyarsa kuwa cewa yayi. "Kuji shegen iyayi, koma mene bake kika jawomin ba, ina zaman zamana kinzo kin tsotseni, jarababbiya kawai, saboda kin zuƙeni ne ae yasa duk zazzaɓin ya hau jikina,  hakanan ina matsayin saurayi, kinzo cikin mintuna kaɗan kin maidani ɗan ƙaramin bazawari."                  Ganin yayi shiru ne yasa Ameena cikin tausayawa  ta gyara masa blanket ɗin, nan ta kashe AC'n da sanyinsa keta busawa,   asanyaye tace.    "Allah ya ƙara sauƙi."      Nan tashiga kimtsa ɗakin nasa, tana kammalawa kuwa ta kunna burner, inda ta zuba turaren wuta mai daɗin ƙamshi, take kuwa ɗakin ko ina ya cika da ƙamshi.      Fita tayi daga ɗakin nasa, kai tsaye ta koma nata ɗakin, wanka tayi  tare da kimtsa kanta cikin riga da sket na atamfa, kana ta yane jikinta da mayafi, flat shoe tasanya, kai tsaye ta nufi ɓangaren Ummi dan zuwa gaisheta, kamar yanda ta saba akowacce rana. Saifuddeen kuwa, bacci ne ya ɗaukesa, don dama daren jiya baiwani samu isashshen bacci ba.               Itakuwa Ameena koda ta ƙarasa ɓangaren Ummi, yau bata iske Ummin a falo ba, saidai ta taradda Raliya wanda ke ƙoƙarin kimtsa falon, kasancewar daren jiya anan Hayatuddeen ya ƙare hirarsa da ciye ciyensa, gaba ɗaya yayi fatali da filullukan kujerun falon, ya watsar su aƙasa, sannan ga ledodin sweet wanda yasha ya zubar acikin falon.      Gaisawa sukayi da Raliyan sannan ta nufi ɗakin Ummi.  Tsayawa tayi ajikin ƙofar tare dayin knocking,  Ummi dake zaune akan gado, jin ana buga ƙofar, yasa ta bada izinin shigowa,  ahankali Ameenan ta tura ƙofar ɗakin ta shiga.   Ganin Ameena yasa Ummi sakin murmushi.  Ƙarasowa cikin ɗakin Ameena tayi, anutse ta durƙusa, cikin ladabi ta gaishe da Ummi'n, nan Ummi ta amsa mata fuska asake, tana murmushi kamar kullum.    Ganin kaya akan gadon Ummi'n, wanda da dukkan alama kayan gugane, yasa Ameenan tashi, cikin nutsuwa ta shiga jerawa Ummi kayan acikin drawer, sosai Ummi kuwa taji daɗin hakan, dan dama tana ƙoƙarin jera kayan kenan Ameenan ta shigo.   Haka Ameena ta gama jera  kayan tsab, inda suke ɗan taɓa hira kaɗan kaɗan da Ummi'n, tana kammalawa kuwa ta sharewa Ummi ɗakin nata, duk da cewa ma ɗakin fes yake, bai wani buƙatan shara, don kuwa Ummi sam batason ƙazanta, kusan awajenta ma Saifuddeen ya gaji ƙamshi da kuma yawan tsabta da ƙyanƙyami.      Koda ta gama  falo ta dawo, bayan tasamu sanya al'barka daga bakin  Ummi'n,  ganin Raliya  a kitchine yasa tayi  kitchine ɗin itama, nan  tashiga tayata aikin breakfast ɗin da takeyi, inda suke hira sosai.           Koda suka kammala kuwa akan dinning suka jere komai, lokacin kusan ƙarfe 8 na safiya kenan, Ahmad ne ya shigo cikin falon, dai-dai lokacin kuma Ummi ta fito daga ɗakinta.     Cikin girmamawa Ahmad ya gaidata,  cikin kulawa, da kuma nuna ƙauna ta amsa masa. Sosai tayi mamakin rashin ganin Saifuddeen a falon, dan kuwa tasan dayaje sallan asuba ya dawo, ita yake fara zuwa ya gaisar, amma saigashi yau bashi babu alamansa, abun dayaso ɗaga mata hankali kenan, dan tasan cewa idan Saifuddeen nada lafiya bazai taɓa kai warhaka baizo ya gaisheta ba, kuma kullum, koda yaushe, a irin wannan lokacin zaka sameshi cikin falon nata zaune. Duban Ameena tayi cikin kulawa tace. "Ameena waini kuwa yau ina Saifuddeen, anya kuwa yana lafiya?." Kai Ameena ta sadda ƙasa, cikin sanyi tace. "Yana ɗakinsa, tun safe yake kwance, zazzaɓi ke damunsa." Cikin matsanancin damuwa Ummi tace. "Subahanallah, zazzaɓi kuma, to yasha magani ne?." Kai Ameena ta girgiza alaman. "A'a" Ahmad dake zaune ne yace. "Nima nayi mamaki dan yau banganshi cikin masallaci ba, kenan ko sallan asuba bai samu yaje ba." Kai Ameena ta jinjina alaman.  "Eh." Cikin yanayin sanyi haɗi da tausayawa Ummi tace. "Nidai nasan cewa hakanan Saifuddeen bazai taɓa kaiwa har iwar haka, batare da yazo ya ganni ba, rashin lafiya ce kaɗai zata ɓoyeshi, muje yanzu ki kaini sashin naku na duba shi." Nan Ahmad da Raliya sukace suma zasu, Hayatuddeen da fitowarsa kenan, jin cewa zazzaɓi na damun hammansa yasa yaji gaba ɗaya hankalinsa ya tashi. Nan suka bi Ameena zuwa part ɗin nasu. Haryanzu kwance yake acikin blanket, dan kuwa zazzaɓin nasa bai ragu ba, saidai kuma ya farka daga ɗan baccin daya ɗaukesa. Ahankali Ameena ta tura ƙofar ɗakin, kasancewar itace agaba. Nan su Ummi suka rufa mata baya. Ganinsa nannaɗe cikin bargo yasa Ummi ƙarasowa cikin sauri, hannu tasa taɗan ɗage blanket ɗin, hannunta takai ta taɓa goshinsa, jin an taɓa goshinsa ya sashi ɗan buɗe idanunsa kaɗan, dan duk atunaninsa mayyarsan ce Ameena.  Ganin Ummi yasa shi ware idanunsa, tare daɗan yunƙurawa ya tashi ya zauna. Cikin kulawa Ummi tace. "Sannu Saifuddeen." Kansa ya jinjina mata amatuƙar shagwaɓe, yana me kallon su Ahmad dake tsaye. Kafaɗansa Ummi taɗan kama, cikin kulawa haɗe da tausayinsa tace. "Sannu meke damunka ne?." Sake shagwaɓe mata fuska yayi, cikin zuciyarsa yace. "Bakune kuka matsa sai na auri wannan Ameenan ba, gashinan jiya duk ta tsotseni, ta rabani da samartaka na, ji yanda take wani wuƙi-wuƙi da ido, ko kunyana ma bataji."    a bayyane kuwa hannun Ummin nasa ya kamo, ya ɗaura akan wuyansa. Nan Ummi taji jikin nasa zafi jau, cikin tausayawa ta dubesa, murya asanyaye tace. "Zazzaɓine ke damunka ko, sannu, yanzu me kakeson ci, idan kaci sai kuwuce asibiti da Ahmad, dan nasan bakasha magani ba." Kwaɓe fuska yayi tare da kamo hannun Ummin nasa ya sanya acikin nasa, idanunsa yaɗan lumshe, gane abun da yake nufi yasa Ummin riƙe hannunsa ɗaya cikin kulawa tace. "Bayan zazzaɓin kuma saime ke damunka!." haka take lallaɓasa kamar wani ɗan yaro. Shikuwa kansa ya ɗaura akan kafaɗanta, inda yasa hannunsa ɗaya ya nuna mata waist ɗinsa ta baya, alaman bayan zazzaɓin nan ke masa ciwo, sannan kuma ya nuna mata jikinsa, alamun cewa gaba ɗaya jikin nasa ma ciwo yake masa. Ɗan jim Ummi tayi tare da ƙuresa da ido, hakanan zuciyarta ta bata wani abu, ɓoyayyen murmushi ta sake, take wani irin daɗi ya cika zuciyarta, hannunta tasanya cikin gashin kansa, cikin yanayin kulawa tace.   "Fine boy ɗina sannu ko, zakaji sauƙi insha Allah, sannan ciwon jikinma zai daina, yanzu faɗamin mekakeson ci, zan dafa ma da kaina." Baki Ameena ta buɗe tana kallon Ummi da Saifuddeen ɗin, tunda take aduniya bata taɓa ganin ƙauna irin tasu ba, wannan salon ƙaunar tasu daban take, musamman idan akayi dubi da irin yanda Ummi ke shagwaɓa Saifuddeen, shikuwa indai yana gaban Umminsa jinsa yake kamar yaro ɗan shekara 3, saboda haka duk wata irin shagwaɓa ta duniya da taɓara ya iyata. Ahmad  da Raliya kuwa murmushi kawai sukayi, dan sunsaba da ganin zallan shagwaɓan Saifuddeen da kuma yanda Ummi ke biye masa, Hayatuddeen kam waje yanema ya zauna. Sake narkewa Ummin nasa yayi, asakalce ya kuma ƙara ɗaura kansa akan kafaɗanta, sai wani ɗan yamutsa fuska yakeyi, saikace wanda shi yayi aikin. Kansa Ummi ke shafawa, duban Raliya tayi kana tace. "Raliya haɗo masa tea, da kuma chips, idan yaci sai su wuce asibiti" Hannun Ummin nasa ya kamo tare da girgiza kansa, cikin body language ɗinsa, yace. "Fruit salad da maltina kawai yake da buƙata." Dubansa Ummi tayi tare da sakin murmushi, nan tace da Raliya takawo masa maltina'n, idan yaso saita koma ta haɗo masa fruit salad ɗin. Hakan kuwa akayi, maltina meɗan sanyi Raliya ta kawo masa,  Ummi dakanta ta ɓalle masa murfin maltina'n, ahankali yakai bakinsa tare daɗan lumshe idanunsa,  cikin ransa yace. "Idan kuwa nasha naji ƙarfi ajikina, ya tabbata cewa wannan Ameenan ba sperm kaɗai ta zuga ajikina ba harda jinina." Ɗago idon da zaiyi kuwa karab sukai ido huɗu da Ameena wanda ta ƙura masa ido, itakam sosai duk wani acting ɗin da zaiyi yake burgeta, yanzu ma haka ji take inama da ace ita yakeyiwa shagwaɓan nan ba Ummyn shiba aima itace matarsa itace ta dace da irin wannan abin da yakeyi. Ɗauke idanunsa daga kallonta yayi, cikin ransa yace. "Wallahi gudunki zannayi, hakanan da ƙuruciyata  bazan amince ki maidani tsoho ba, daga zuwa ɗaya har kinsani rashin lafiya, next kuwa inaga ko tashi bazan iya ba, da wani idanunki awajen ai kin san dai bani da lfy." Yaƙare zancen zucin yana ɗan hararan gefenta. Ahmad kuwa duk abun da Saifuddeen din keyi yana lure dashi, hakanan yasaki wani irin dariya, wanda yasa Saifuddeen ɗin watsa masa harara, cikin ransa yace. "Ehem dole kayi dariya ae, tunda kafahimci cewa mayyar da kuka haɗani da ita, tun ba'ayi nisa ba tafara tsotseni."    Idanu Ahmad ya kashe masa alaman, yane?  laɓɓa SAIFUDDEEN ɗin ya ciza, tare da jinjina kai, alaman zasu haɗu ne. Ummi kuwa murmushi take, dan tagama fahimtan komai, tabbas tasan cewa Saifuddeen baison wahala ko kaɗan, wannan dalilin shiyasa ma wata ƙila zazzaɓi ya sauƙar masa. Yana gama shan maltina'n Raliya ta kawo masa, haɗaɗɗen fruit salad wanda yaji madara. Balaifi ya ɗan sha, ya kuma ji daɗin bakinsa. Dubansa Ummi tayi cikin kulawa tace. "Kasamu kayi wanka, kuje asibiti likita ya dubaka, ko kuma ma zan ƙira Dr Adnan kawai yazo ya dubamin kai agida." Tana gama faɗan haka ta miƙe tsaye, nan ta fice daga cikin ɗakin,  kana Raliya ma ta rufa mata baya. Ahmad ma binsu yayi, Hayatuddeen kuwa hannun Hamman nasa ya kamo, cikin kulawa yace. "Sannu My lovely Hamma Allah yabaka lafiya." Kai Saifuddeen ya jinjina masa alaman "Ameen." Nan Hayatuddeen ɗin ya miƙe yafice daga cikin ɗakin. Ajiyar zuciya Ameena ta sauƙe, tare da takowa taƙaraso kusa dashi, zama tayi agab dashi, cikin kulawa ta kamo hannunsa,  fuskarsa ta shafa tare da cewa. "Ya jikin naka?" Kansa yaɗan jinjina mata, alaman. "Dasauƙi"  tare da ɗan mako hannunta yayi kissing bayan hannun, sannan ya janye fuskarsa  baya. Jawo wheelchair ɗinsa yayi ya hau, ahankali ya tura kansa zuwa toilet. Ajiyar zuciya Ameena ta sauƙe, hartayi tunanin binsa cikin toilet ɗin kuma saita fasa,   nan dai tayi kwance akan gadon, lumshe idanunta tayi, tana me tuno moment dinsu na daren jiya, hannunta takai kan mararta, asanyaye tace. "Ya Allah kasa adaren jiya nasamu rabo daga Saifuddeen, tabbas kuwa da sainafi kowa farinciki, domin samun iri daga Saifuddeen babban abun al'fahari ne,  sannan kuma zan zama kamar zara acikin taurari, dan haihuwa da Saifuddeen babban nasara ce, ya Allah kabani ɗa ko ƴa me kama dashi." Cikin farin ciki ta amsawa kanta da "Ameen." Saifuddeen kuwa balaifi yaɗanji dama, sake wanka yayi tare dayin brush, nan yafito jikinsa duk danshin ruwa, harzuwa lokacin Ameena na kwance, kasancewar wani ɗan bacci-bacci ne ke fusgarta. Tsane jikinsa yayi, inda ya shirya kansa cikin wasu lafiyayyun riga da wando ƴan kanti masu tsadar gaske, sosai yayi kyau cikin kayan,  wankan turare yayiwa jikinsa,  wasu baƙaƙen toms yasanya aƙafansa, masu kamar combat, gashin kansa sai ƙyalli yake, wayansa ya ɗauka, nan yaƙaraso jikin gadon, ahankali yaɗan leƙa fuskar Ameena, gani yayi ma baccinta take cikin kwanciyar hankali. Kansa ya jinjina tare da yin ɗan murmushi cikin zuciyarsa yace. "Badole kiyi bacci ba, tun da dai daren jiya kinsamu ɗan bawan Allah kin gurza."   tura kekensa yayi inda ya fice daga cikin ɗakin. Cikin nutsuwa ya nufi part ɗin Ummin nasa, koda Ummi tagansa taji daɗi sosai, duk da cewa zazzaɓin baisakesa duka ba amma dai yaɗanji sauƙi, kwanciya yayi afalon, Ahmad dake zaune afalon ne ya matso kusa dashi. Duban Saifuddeen ɗin yayi cikin ƙasa da murya yace. "Ango kasha mai, to yaya yakaji auren da daɗi ko?" Cikin takaici Saifuddeen ya ɗauki pillow'n kujera ya gwaɗawa Ahmad ɗin, dariya Ahmad yayi, tare da cewa. "Daga faɗan gaskiya kawai, ai kuwa dai wannan amarya taka jaruma ce, saboda haka ka ƙara riƙeta da kyau, kaikuma saika tsaya adubaka,  saboda dai yanzu kam kafita sahun saurayi kadawo bazawari!." Cikin tsokana Ahmad ya ƙare maganar, sanin cewa ya hasala Saifuddeen ɗinne yasashi matsawa gefen cikin sauri, dan yasan yanzu Saifuddeen ɗin zaikai masa duka. Saifuddeen kuwa sosai ya ƙulu, hakan yasa yadinga cije laɓɓansa, yana hararan Ahmad, Ahmad kuwa mezaiyi inba dariya ba. Suna haka Dr Adnan ya iso, dan Ummi taƙirasa, inda tasanar dashi matsalan Saifuddeen ɗin. Sosai Dr Adnan din yayi checking dinsa, ganin komai lafiya yasashi, rubutawa Saifuddeen ɗin magunguna, nan ya miƙawa Ahmad yace "Yaje pharmacy ya sayo."   bakomai yasa masa zazzaɓin ba kuwa face, yanayin daya samu kansa aciki wanda bai taɓa ba, hasali kuma hakan yafarune bawai don bashida lafiya ba,  ko wasu masu lafiyan sukan samu kansu cikin irin condition ɗin da Saifuddeen yasamu kansa,  musamman idan hakan yazama shine farkon fara sex ɗinsu, sannan hakan na faruwa idan Namiji yaɗauki tsawon lokaci yanajin sha'awa, sannan kuma bai samu yayi sex ba, to aduk lokacin da yayi sex da mace, yana zubar da sperm zazzaɓi  me zafi zai iya rufesa, wanda kuma zai iya sauƙa akowani lokaci. Nan dai Dr Adnan yayi masa fatan sauƙi daga, haka yayiwa Ummi sallama ya tafi. Cikin mintuna kaɗan kuwa Ahmad ya kawo maganin, shida kansa ya bawa Saifuddeen din magungunan yasha. Haka dai Saifuddeen ya ƙare, gaba ɗaya wunin yau  a part ɗin  Ummin sa, ba laifi kuma yaji sauƙin jikinnasa sosai.            Can cikin Gombe State University kuwa Hayatuddeen ne ke zaune acikin class, inda gaba ɗaya fiye da rabin ɗaliban ajin nasu ke waje, kasancewar sun ƙarƙare lecture ɗinsu na wannan ranan,   can ƙarshen benci yaje ya takure kansa, wayarsa ƙirar iphone 8+ ne ahanunsa, yayinda ya saƙala earpiece akunnensa,  gaba ɗaya yaba da hankali haɗi da nutsuwarsa ga wayarsa, da dukkan alama wani abu yake kallo wanda ya ɗauke masa hankali.            Khamis dake tsaye akansa tun ɗazu batare da, Hayatuddeen din  yasan da zuwansa ba ne yasaki dariya, azabure Hayatuddeen ya ɗago kansa, ganin Khamis yasashi, sakin wata irin ajiyar zuciya me ƙarfi, aɗan hasale yace.  "Mcheeww wallahi Khamis kai banza ne ji ka tsoratani."      Murmushi Khamis yayi tare da zama agefen Hayatuddeen ɗin, hannu yasa ya dafa kafaɗan sa, dubansa yayi tare da cewa.    "Kai wallahi tsoronka yayi yawa, menene to acikin BF da har ma sai ka ɓuya kake kallonsa, hmmm yaro inzakasha giya kasha ta dubu, kaine har yanzu kanka bai gama wayewa ba, har yanzu fa baka iya ko riƙe hannun mace, iya iskancinka ya ƙare a waya, daga anyi magana kace kai bazaka iya ba, mufa yanzu mune manyan gobe, yanzu ne ya kamata ace munci ƙuruciyar mu, mun shana, sannan muyi abun da mukeso."            Iska Hayatuddeen ya fesar ta bakinsa,  girgiza kansa yayi tare da   cewa.                   "Bazan iyaba Khamis, ni sam bazan taɓa iya aikata haka ba, insha Allah har duniya ta tashi bazan taɓa yarda nakusanci zina ba, kasan girman zunubin wanda ya aikata zina kuwa Khamis?  hmmm nikam dai ba ruwana, iskancina a iyaka waya ya tsaya kamar yanda ka faɗa da farko, amma taɓa jikin wata mace, wanda ba muharamma ta ba gaskiya bazan iya ba."      Hararansa Khamis yayi tare da cewa.  "Shiyasa nace bazaka taɓa wayewa ba, yanzu mene amfanin kallon BF matuƙar bazakanemi inda zaka gusar da sha'awan ka ba? hmmm nidai wallahi shanawa ma yanzu na fara ehe."      Murmushi kawai Hayatuddeen yayi tare da playing vedio'n sa ya cigaba da kallo, yana mejin wani irin abu acikin jikinsa, sau dayawa yakanji kamar ya daina kallo, amma kuma zama da Khamis yasa kallon BF ya zame masa tamkar wani kallon film, yayi sabo da ganin BF sosai, saboda haka koda yace zai daina sai yaji ya kasa, duk da cewa yasan kallon BF din ba kyau, amma sosai idan yana kallo yakejin kansa cikin wani irin shauƙi, saboda  yanajin cewa shima yanzu yazama saurayi shekara 20 da yake dasu, sunsa yanajin kansa kaman ɗan 30 years. Shida kansa yasan da taraiyar sa da su Imran tafi mishi daɗi da al'khairi to abin ta kaicin Imran F.C.E yake Sulaiman kuma da Isma'il Kashere University suke. Zakariyya kuma da yake nan cikin G.S.U ɗin sai kuma ya kasance Department ɗinsu ba ɗayaba, tofa wannan dalilin ne ya rabashi da tsoffin abokansa a makaranta ya haɗashi da wannan ɗan banzan khamis ɗin mai ƙafafu kamar faskaren wawa. Wannan yana ɗaya daga cikin illar abokai, dole iyaye mu lura da abokan yaranmu muddin sun fara tasawa. Zakiyi shekara 14 kina bawa ɗanki/ƴarki tarbiya mai inƙanci to. Tofa daga shekara 15 zuwa 18 akai ashirin zaki fara yaƙi da gasa da abokanshi da zasu fara bashi tasu tarbiyar da in kinyi sakaci da addu'a dasa ido cikin awa ɗaya zasu kore taki tarbiyar nan su ɗaura tasu, shike nan sunyi nasara a kanki sun cuci rayuwar yaronki damake kanki, hattara garemu iyaye mu kula...! Tashi tsaye Khamis yayi tare da cewa.    "Saika tayi ae, kazauna nan a haka kada ka nemi ƙarin wayewa akan wanda kake dashi, ni kaga ma tafiyata, saboda yau ƙarfe 7 dai-dai muna da wani show me zafi a night club, nasan ma idan nace kazo ba zuwa zakayi ba."                   Kai Hayatuddeen ya jinjina tare da cewa.        "Saimun haɗe gobe, danni ma nasan driver ya kusa zuwa ɗauka na,  aje night club lafiya amman banda ni kam, bazanci amanar hamma da Ummynmu ba."        Dukan wasa Khamis ya kai masa, sannan ya juya ya fice daga cikin class ɗin.                  Bawani jimawa shima Hayatuddeen ɗin, sule driver yazo ya ɗaukeshi.                            Ƙarfe takwas na dare dai-dai  yadawo daga masallaci, kaitsaye part ɗinsa ya wuce, kasancewar akwai wani aikin sirri wanda zai gabatar, domin ansashi binciken wani riƙaƙƙen ɗan fashi, wanda ya addabi mutane, sannan kuma har zuwa yau ankasa gano inda yake, saboda hakane ma aka danƙawa Saifuddeen ɗin ragamar case ɗin ahanunnsa, kasancewar sun san ya ƙware wajen iya computer, da computer kaɗai zai iya gano musu inda mutumin yake.           Yana  shiga ɗaki kayan jikinsa ya soma ragewa, inda ya zauna daga shi sai 3 guater da kuma farar singlet, laptop ɗinsa ya jawo tare da sanyata  gaba, nan ya maida gaba ɗaya hankalinsa ga aikin da yakeyi.              Da misalin ƙarfe 9 kuwa Ameena tashigo cikin ɗakin.    ganin cewa yana gudanar da aiki me mahimmanci,  yasa batayi ƙoƙarin damunsa ba, kan gado kawai ta ɗale tare da kwanciya, sama-sama taɗan latsa wayarta daga haka bacci ya ɗauketa, ko data'n ta dake akunne bata kashe ba.     Shikuwa Saifuddeen har wajen 12 na dare yakai yana aikin bincike, cikin sa'a kuwa yagama haɗa duk wani information da yake so, dan kuwa ya gano inda mutumin yake, saida ya turawa ogansu komai kafun yake rufe laptop  ɗinsa, nan ya ɗauro alwala sannan yazo ya kwanta, ganinta haka bata rufe jikinta ba, yasashi rufa mata blanket, tare da gyara mata konciyarta, cikin mintuna kaɗan bacci ya ɗauke sa.       Washegari kuwa ya tashi da ayyuka masu yawa akansa,  hakan yasa tunda ya fita daga gidan bai dawo ba sai wajajen 3pm,  nan ma dai part ɗin Ummi ya zauna.   Koda dare yayi ya tafi zuwa ɓangaren su, nan yasamu Ameena har tayi bacci, yaji daɗin hakan kuwa, don dama baiso ya isketa idanunta biyu, gudun kada ta ce zata ƙara neman wani abu daga garesa.               Aikinsa ya ɗan taɓa kafun bacci ya ɗaukesa.        Yauɗin ma dai baitashi da niyan zaman gidan ba, dan yanzu aikin nasa yaɗau zafi wani abun dole sai ya fita da kansa yaje ofishin sirri na DSS.   Cikin nutsuwa yagama kimtsa wa, cikin wani lallausan yadi me kyau da tsada, yayi kyau matuƙa, Ameena dake tsaye tana kallonsa ne tasaki murmushi, tare da ƙarasowa kusa dashi,ido ya ɗan zuba mata ganin ta sunkuyo kanshi a hankali ta dai-daita fuskarsa da nata, batare da yayi  aune ba sai kawai jin bakinta yayi, acikin nasa tanayi masa tsosan sweet,  sam bai hanata ba saboda haƙƙin tane, saidai kuma baiwani biye mata ba, cikin mayen soyayyarsa ta ɗago idanunta ta kallesa, kallo ɗaya yayi mata yaɗan ɗauke kansa, murmushin yasakar mata tare da shafa gefen fuskarta, cikin body language ɗinsa yayi mata alama kan cewa. "Saiya dawo." Fatan al'khairi tayi masa, yana fita tafaɗa kan gado, tare da sakin ajiyar zuciya.        Shikuwa  Saifuddeen saida ya biya ta wajen Umminsa kafun ya fito, inda sule driver yayi driving ɗinsa suka fice daga cikin gidan. Ameena kuwa yau a ɓangaren Ummi ta wuni, ba ita ta koma sashinsu ba sai da magrib ta gabato.       Tanayin sallah kuwa ta ɗauki tsumin ta ta sha, tare da turara jikinta da turaren ƙamshi. Nan dai ta kimtsa kanta tsab, dan tana matuƙar begen mijinta, kwana uku kacal amma tayi mugun missing lallausan jikinsa.      Duk da cewa ya jima da dawowa amma bai shigo gidan ba saida  yayi sallan Isha, ɓangaren Ummi yaje suka ɗan taɓa hira, kafun ya komawa part ɗin nasu.         Yana shiga ɗakinsa ya iske Ameena zaune akan gado, tasha ado cikin sleeping dress masu kalar pink.                 Yau ita da kanta ta haɗa masa ruwan wanka.  Koda ya fito daga wankan, amsan towel ɗin hannunsa tayi, nan tashiga goge masa ɗan danshin ruwan dake jikinsa, haka dai yaɗan kimtsa inda ya hau kan gado ya kwanta. Itama Ameenan kwanciya tayi akan gadon, tare da  zagayowa ya zama suna fuskantar juna,     ɗan ranƙwafowa tayi tare da kamo hannunsa ta ɗaura akan waist ɗinta,   bakinta ta ɗaura akan nasa,  inda ta kamo laɓɓansa tana sucking,  lumshe idanunsa yayi cikin ransa yace.   "Oh ni Saifuddeen naga takaina, nadawo kaman wani alawa, ko yaushe tana cikin tsostsotseni ita ko gajiya ma batayi ne."      Ameena kuwa gaba ɗaya ta fara manta inda take, sosai take romancing ɗinsa,  gane abun da take nufi yasashi, kasa hanata abun da takeso, saboda haƙƙinta ne, idan ya hanata sai Allah ya tambayesa.                     Kamar dai wancan daren haka awannan daren ma Ameena ta more Saifuddeen, Ido ya lumshe dai-dai lokacin data zauna kan cinyoyinshi suna fuskantar juna, Zaleeha yake jida gani a cikin jikinshi da zuciyarshi, shiyasa a take lafiyarshi ta harba ya miƙe ƙam yana ta harbawa da cika, Ajiyan zuciya ya sauƙe da ƙarfi jin ta haɗe kanta dashi, yana mai mmkin duk abinda fa  Ameena zata mishi baya tashi har sai dai in ya tuno Zaleeha ya kawota cikin ransa, Haka nan yake jin tausayin Zaleeha dan wallahi Allah yasan karonta dashi bazai mata ta daɗiba, ya guturta kashe bakin tsiwar nan a dare ɗaya, yanaji a jikinsa tabbas Zaleeha matarsace zata dawo da ƙafafunta zai kuma yi maganinta yana dai-dai ƙugunta, a haka dai yana cikin tunanin Ameena tayi ta bidirinta a jikinshi, ido ya ɗan lumshe sai da aka ɗan zo bakin boda ne, sai ya jawota jikinshi ya ruggumeta da ƙarfi tare da sauƙe tagwayen numfarfashi. Dan gane da gajiyar jiki kuwa, sai ma abun daya ƙaru, don kusan yau zaice yamafi ranan jin gajiya, sam bayason wahala, bazaice Ameena bata gamsar dashi ba, sannan bazaice bayajin daɗin kasancewa da ita ba, saidai ajikinsa yanajin tabbas akwai wani  babban gurbi wanda bata iya cikewa, hakanan yakeji kamar akwai wani abun da ta rasa baijin irin gamsuwar da yake buƙata ba, hakan kuma baya rasa nasaba da bata iya jure tsawon lokacin da yake buƙata, yana buƙatar gamsuwa ta sosai da sosai ita kuwa Amina macece dole tanada rauni.          Wanka yayi sannan ya dawo ya kwanta, ajiyar zuciya yaketa sauƙewa dan yagaji sosai, itama Ameenan kwanciya tayi bayan tayi wanka, haka takejin ranta ƙal, bata da wani sauran damuwa. Hannunshi ya ɗan sa a hankali ya s....! *Uhummm yanzu aka fara kabcen, ana dara sai ga dere yayi, ƙaƙa tsara ƙaƙa!?.* LITTAFINA NA KUƊINE duk wacce ya/ta karanta bata biyaba tasan na ne ta karanta, ɗari ukune dai nace kuɗin ba miliyon uku ko dubu ɗari uku ba ko dubu ukuba ɗari uku zaki turo katin mtn na 300 ta number nan 09097853276 ko kimin transfer 300 ta asusuna na 0005388578 jaiz bank Aisha Aliyu Garkuwa, sai ki turo shaidar biyanki ta no nan 09097853276 By *GARKUWAR FULANI*