💋❤️AUREN HUCE HAUSHI.💋❤️ MAMAN FATIMAH. DA SUNAN ALLAH MAI RAHAMA MAI JIKAI SALATI DA DAUKAKA DA AMINCI SU TABBATA GA FIYAYYAN HALITTA ANNABIN RAHAMA MUHAMMAD BIN ABDULLAHI DA ALAYENSA DA SAHABBANSA WANDA SUKA BISHI HAR ZUWA TASHIN ALQIYAMA. Wannan littafin kifkirarran labari ba'a yishi Dan wani ko wata ba duk abinda akaci karo dashi Arashi ne kawai. This Book is dedicated to you Ten sisters. Allah ya Kara Mana zumunci. Paga one ..........A hankali motar da shigo layin dai dai wani katafaren gate ta tsaya, yanayin yanda take fidda wani Dan Kara alamune dake nuna motar tayi dogon zangon tafiya, direban Bai Danna Horn ba bara a kaiga bude gate din gefen wata bishiyar dorawar tururawa ya karasa da motar, wasu dattawa ne su buyi suka fito daga bayan motar yayin da wani matashi ya fito daga mazaunin direba, Mika yayi dareban tare da salati. Kofar gidan suka nufo da kafarsu Dan matshin be yayi nocking kamar day biyu kafin wani dattijo ya leko ta wata karamar kofa jikn gate din. Da sauri ya bude kofar Yana fadin "A'a Alhaji barkan ku da zuwa kin Sha hanya sannunku" tare da Basu hannu sukayi musabiha suna fadar "wlh kuwa malam Sani ya muka sameku?". Cikin fara'a yake fadar "Alhamdulillahi". Kafin yayi gaba Yana cewa "Bari nayi Muku iso gurin Alhajin Allah ya taimaka Yana nan". Harabar gidan suka shiga suka rufawa malam Sani baya zuwa bangaren Mai gidan inda yake ganawa da bakinsa. Lokacin da suka karaso gurin kofar shi Kuma Malam sanin ya fito Yana fadin "Bismillah ku shiga, sannunku". Yayi gada da sauri Dan cika umarnin Alhajin na Kiran babban Amininsa na kankankan Malam Bukar. Da sallama suka shiga falon, Masha Allah komai najin dadin rayuwa akwai shi a falon tamakar fadar wani sarkin. Cikin fara'a da sakin fuska Alh Jafar Mai Yadi ya nufo bakin nasa Yana fadar "A'a! Alhaji Sulaiman kune haka cikin wannan ranar ga nisa". Amma kasan zuciyarsa mamaki ne fall a cikinta shi dai yasan ba wani abu daya taso da zai kawosu a irin wannan lokacin a kalla suna da sauran kwanaki uku kafin duzo duk da sun bada duk abinda ake da bukata lokacin kawai ake jira. Amma dai ko meye Allah yasa Alkhairi ne. Bayan gaishe gaishe na al'ada daya daga cikin 'ya'yan Ahj Jafar ne yayi sallama ya shigo Yana gaishe da bakin Yana aje musu lemon da ruwa ya fita. Wani matashin ne shima ya shigo da manyan warmers da wata yarinya da basket Mai dauke da plates da cokula da cups Suma suka gaishe dasu suka fita. Tunda aka Fara shigo da wannan karamar arzikin Alhaji sulaiman ya sadda Kai kasa zuciyar idan tayi dubu to a bace take. "Bismillah kuci abinci kafin mu shiga sallah tunda Azzahar ta gabato". Alh Jafar ya fad'a Yana nufar kofar fita. Bayan fitar Alhaji Jafar Alhaji Ismail ne ya kalli Yayansa Alhaji sulaiman "Nifa duk na rude wallahi har na rasa ta inda zamu Fara fad'a musu irin wannan magana duba da irin karamcin wannan bawan Allah". Ya fad'a yana Jan siririn tsaki. Dan matashin daya tukosu ne yayi magana "wlh Daddy naso kun hakura da zuwa ita Hajiyar tazo da kanta ta fad'a musu abinda ta kulla, ni ban taba ganin irin wannan ba anyi Abu cikin mutunta juna har an kawo wannan gabar Amma Rana tsaka irin wanna ta taso Babu Dadi ni wallahi tausayin Musbahun nakeyi ya shiga wani hali Amma ita ko a jikinta". Shi dai Alhaji sulaiman Bai Kara magana ba haka Bai ko kalli abincin ba duk da yunwa da yakeji leonm da ruwa kawai ya sha, Alhaji isma'il da Al-Amin ne sukaci abincin suka fita zuwa masallacin kofar gidan. Tare suka shigo gidan bayan idar da sallar har da Malam bukar domin shine limamin masallacin. Sabuwar gaisawa suka karayi Amma wannan lokacin Al-Amin Bai biyosu ba. Alhaji sulaiman ne yayi Qarfin halin Fara magana Yana kallon Malam Bukar "Dan Allah malam ayi hakuri da abinda mukazo dashi WALLAHI badan Nan gidan bane Babu abinda zai Kara dawo Dani garin Nan". Yayi shiru ya kasa karasa maganar saboda wani abu daya tsaya Masa a makogwaronsa yana masa tukuki. Shima Alhaji Jafar wani abune ya tsirga masa har tafin kafarsa ga wata irin faduwar gaba taba gaira ba dalili. Shiru falon ya dauka na wucin gadi kafin Malam Bukar ya magantu "Alhaji ka Fadi ko menene ba wata matsala ita rayuwa ba yanda Bata zuwarwa bawa ko Dadi ko akasin hakan, Kuma duk musulmin kwarai ai yasan kaddara, ba damuwa ai and Zama daya". Alhaji Ismail ne ya karbi maganar ganin yayan nasa bashi da niyyar cigaba da maganar. "Ayi hakuri Malam kan maganar auren yaron gurinmu ne da yarinyar gurinku, wata fitina ta taso yau kwana uku kenan ana Abu daya mahaifiyarsa ta kafe kaida fata Bata amince ya auri Zahra ba duk yanda mukaso gyara abun ya gagara karshe ma cewa tayi idan har Musbahu ya auri Zahra Bata yafe Masa nononta daya sha munyi munyi da fad'a Mana dalilinta na wannan cin zarafin Amma ta kekashe taki fad'a karshema abun ya zamar Mata lalura kamar ta jinni". Tunda ya Fara kora bayani Alhaji Jafar ke maimaita Innalillahi wa inna ilaihi raji'un, domin duk wani karfin gwaiwarsa ya Kare wannan wace irin musiba ce kullum idan auren yarinyar nan ya taso sai an Sami wani akasin ya taso shi Lamarin Nan ya rasa yanda zeyi dashi. Malama Bukar ma rasa abin fad'a yayi duk wani kuzarinsa ya Kare. Yayin da su Alh Sulaiman suketa nanata ban hakuri. Cikin muna juriya da dattako Malam Bukar yace "haba Alhaji ba komai kasan komai nufi ne na Allah Daman Bai Qaddari shine mijinta ba, Allah yasa hakan yafi musu Alkhairi su duka'. Gaba data suka amsa da Amin. "Amma dai Abu baiyi Dadi ba wallahi ba Baki nayi musu ba Amma kafin a Sami Mai nagaratr yarinyar Nan zasu Dade suna nema" cewar Alhj Ismail. Har gurin mota suka raka bakin, har suka daga bakinsu Bai Dena bada hakuri ba. Bayan tafiyarsu falon su Malam suka dawo jiki a sanyaye duk Lamarin ya cakule wannan wace irin kaddara ce ke bibiyar karamar yarinya haka aure dai dai har uku ana fasawa. Cikin nuna damuwa Alhaji Jafar ya kalli Malam Bukar yace "malam inshallah Allahu wannan karon zan aurar da Fatima tunda Naga lamarin bana arzki bane ko meye in Sha Allah sai Naga bayansa'. Tunda Alh ya Fara magana Malam Bukar ke girgiza Kai shima lamarin ya kaishi makura yasan lamarin yarinyar akwai magauta a cikin Amma ganin an samu rata Mai yawa a tsakani ya dauka abun ya wuce ne. Cikin nuna alhini Malam ya kalli amininsa yace "Dan Allah Alh kayi hakuri kada kayi Abu cikin fushi da kace zaka aurar da ita kada azo ayi aikin Dana sani". Kujerar dake daura da Malam din ya zauna kafin ya sauke ajiyar zuciya. "Ko daya banyi fushi da ikon Allah ba kawai dai na gaji da wannan wasan ne kullum na Zama karamin mutum saina Raba I.V na daurin sure azo ace an fasa wasu ma sai su zageni ace Dan bani na haifi Fatima ba na saka ido ana Mata wannan cin zarafin wlh da banyi alkawarin daina hada auren zumunci ba da yau ba sai gobe ba zan aurawa Abdul Hakeem ita. Amma yanzu ma Bata baci ba ka nemi shawarar Mahmud na Nan gurinka idan ya amince na bashi auren ta". Cikin kaduwa Malam Bukar ya kalli Alh Jafar yace "Wane Mahmud din, ba dai na Nan gurina ba?". Cikin yadda da Kai Alh Jafar yace "shifa nake nufi ko akwai wani Mai wannan sunan a gurinka?". Gargiza Kai Malam din yayi tare da fadar "Babu, Amma Alhaji al'marin Mahmud ba boyayye bane a gurinka kada duniya ta zagemu fa". Gyara Zama Alhajin yayi kafi ya fuskanci amininsa sosai. Wallahi Malam bana gudun duk abinda za'a fad'a na yaba da nutsuwarsa idan kaga ba'ayi ba to shima Allah Bai nufi mijinta bane Amma na jima Ina yiwa 'ya'yana sha'awarsa". Kai kawai Malam yake jinjinawa shi lamarin duk yazo Masa a baibai ya jima Yana nazari akan lamarin Fadima kullum Abu daya yake gani mijinta ba Nan kusa take ba bil hasal ma wani lamari yake gani Mai girma dangane da mijin nata da wani irin Haske Amma koda Wasa Bai taba fadawa Alhajin ba sai dai Yana yawaita saka almajiransa gurin yi Mata addu'a. Sun jima suna kullawa da kwancewa a tsakaninsu daga karshe suka tsaya a malam ya tambayi ra'ayin yaron idan yana so la'ba'as. _______ A hankali take sakkowa daga stair din tamkar wani dawisu Tasha make-up da wata gawon Mai azabar kyau Sai karamar pos a hannunta daga bayanta 'yan Mata ne su biyu ko wacce Tasha nata gayun, tun kafin su karasa sakkowa kamshinta Mai saka nutsuwa ya gauraye ilahirin falon. Falon a Cike yake da jama'a kowa ka gani ta amsa sunanta sai tsirarun yara. Da sauri wata ta matso gurin su tana rangada buda, tana fadar "Masha Allah Amarya Allah ya kade hau da bala'i ya bada zaman lafiya Hajiya Zahra suga bayi farin banza jikar hardon fulanin Mubi jikar larabawan Jodan da larabawan madinatul munawwara kaga musu kyawun asali Amarya a gidan Mushahu alherin Allah yakai Miki". Wata daga cikin matan dake zaune ta tashi ta sunga zubawa marokiyar kudin ita Kuma tana Kara Koda Amarya Zahra. Aunty Hasana ce ta fito daga wani Dan korido ta karaso tana kallon kanwar ta ta, tana Kara tasbihi ga ubangiji daya halicci wannan kyakykyawar surar. Hannaun Zahra ta rike tana kallon Baba Tabawa Mai aikinta yanda ta zage tana jero kirari kamar wata marokiya. Dan murmushi tayi tana fadar "Masha Allah, Baba Tabawa yaushe Kika Zama marokiya bani da labari?" Dariya tayi tana fadar " ai ko ban iya ba na koya mu Abu namu bikin uwar dakina guda kinsan biki na d farar kaza balbela ba gayya ce ba, yakuwar kan kabari kenan baking cikin 'yan taushe, murucin kna dutse Baki fito ba sai da kika shirya" Dariya sukayi gaba daya, har gurin da zasuyi bridal shower din kawar Aunty Hasana da Baba Tabawa suka raka Zahra. Sun chashe, sunyi hotuna kamar ba gobe sai dai duk Wanda yasan Zahra yasa Bata cikin walwala haka nan take Jin wata irin faduwar gaba da rashin dadin zuciya Amma ita kanta Bata San taka maimai me yake damunta ba gashi tun jiya take neman wayar Mushahun ta kasa samun shi, haka ta abokinsa Deeni itama shiru a yanda sukayi dasu yau ne ranar da zasuzo Dan har hotel din da zsau zauna sun Kama mukullan ma suna hannun magaji. Dadin dadawa yau sukayi za'a kawo ya'yan yayar shi da wasu cussing dinsa. Sai gurin karfe Tara suka Gama shagalinsu, Zahra Bata koma saman ba inda akayi musu masauki Sai ta nufi bed room din Aunty Hasana na kasa dakin ba kowa sai kamshin freshner da turaren wuta yake tashi ga danyi AC ya gauraye dakin. Head din ta cire ta aje kan bed side locker kusa lamp, gadon ta hau ta kwanta lamo kamar ba mutum akai Dan ko kwakwkwarwn motsi Bata sonyi wata irin kasala ce ta sauko Mata. Ta jima a dakin kafin taji alamun bude kofar Bata daga Kai taga ko wanene ba kamshin da taji ne ya sanar da ita Auntyn ce. Kusa da ita ta zauna tana Kai hannu jikin.wuyanta tare da tambayar "me yake damunki? tun safe Ina Kula da mood dinki Sam bakya cikin nutsuwa". Ta fad'a tana kafe Zahrar da Ido. Yunkurawa tayi ta tashi zaune tare da fadar "Nima bansan me yake damuna ba wlh Aunty Sam bana Jin dadin zuciya ta sai zafi take min Kuma gabana sai faduwa yakeyi". Ta karasa fad'a tana shashhshekar kuka kasa -kasa. "Meye Kuma abin kuka? keda zakiyi farin cikin Allah ya kawo lokacin bikin ba kamar lokutan baya ba da aka dunga samun akasi". Kanta ta kifa a jiki Auntyn taci gaba da kukan ta marar sauti. Bata hanata sai tayi Mai isarta kafin ta Sami zarafin magana. "Aunty wlh Ina ji a jikina kamar wannan ma za'a Sami matsalar kinsan jiya saida nayi irin mafarkin da nakeyi idan za'a fasa aurena". Ta fad'a tana Kara goge kwallar data ciko Mata Ido. Kallon ta kawai Aunty Hasana take ita fa lamarin yarinyar Nan Yana Bata tsoro kada fa namijin Aljani ya aure ta suna zaune Basu Gane ba. Karo biyu ana saka bikinta abun Yana lalacewa toga wannan ma, itama fa kawai daurewa tajeyi tunda Zahra ta fad'a Mata Musbahun Bai kira ba Bai kumazo ba ba wani Kuma nasa da yazo alhalin ba haka aka tsara abunba, Amma sai tayi ta maza tace. "Haba Zahra ya Zaki ringa fadar irin wannan maganar kiyi addu'a ba abinda zai Sami aurenki wannan karon sai Alkhairi, Ina ga da abinda ya hanasu karasowar har yanzu ki jira zuwa gobe Mana maza kiyi sallah kici abinci a sakonki can ki dauko zuwa an jima sai kiyi amfani dashi. _________' GIDAN MLM BUKAR Bayan idar da sallar insha'i Malam da sauran manyan Almajiransa suna Zama ana karatun littatafan fiqihu da hadisan Manzon Allah s.a.w.w, a Nan cikin baban falonsa ake karatun an kwata shi sosai a zuba kujeru na alfarma, saida aka Gama karatun sannan sukaci abinci kamar yanda aka Saba kafin Kuma kowa ya nufi nasa gurin duk da makarantar ta Sami cigaba sosai kamar ba makarantar amajirai ba anyi Mata tsari sosai a zamanace Dan har hostel garesu sama da kasa da gurin koyon sana'a Kuma ana musu abinci basa zuwa bara, sannan akwai malamai da aka dauka suna koyar da karatun boko tun daga mataki primary, junior, zuwa senior, secondary suna kokarin Fara turo dalibansu zuwa manyan makarantu, sun Sami wannan cigaban ne karkashin wata kungiyar NGO ne. Lokacin da Mahmud da Habib zasu fita Malam yayi gyaran murya duk su biyun suka juyo, Mahmud yayiwa alama daya dawo shi Kuma Habib ya fice.. Nan kusa da Malam ya zauna ta lakwashe kafafuwansa kamar zaman daukar karatu. A hankali Malam yake Kare masa kallo shi kadai yasa abinda yake kissimawa a zuciyarsa sai Kuma Allah daya hallice shi. Sun dauki kamar minti uku a haka kafin Malam ya magantu. "Mahmud" Malam ya Kira sunansa. Cikin ladabi ya amsa Masa da "na'am Malam". "Kasan dalilin dayasa nayi kiranka?". Cikin ladabi ya amsa da "A'a" Cikin wani irin yanayi Malam yace "wani nauyin Kuka aka Dora min Wanda na rasa ta inda zan Fara maka bayani". Zamansa ya gyara Yana Kara fuskacin Malam din Yana fadin "Malam ka fad'a min ko menene ni maiyi maka biyayya ne In Sha Allah". "Ai kasan gidan Alhaji Jafar nawa za'ayi bikin yarinyar gurinsa ko?" Kai ya gyada Masa tare da cewa "Eh na Sani ba Zahra za'a aurar ba?" "Eh ita fa, to an samu wata matsala ne wadda ta haddasa kasa auren a wannan karon ma kamar lokutan baya Amma wannan sai yafi na bayan Muni domin kuwa saura ba kaiwa ga Fara bikin Amma wannan Saida abun ya kurace har an saka yarinyar a lalle sun Fara duk kwaramniyar su ta Mata a lissafi saura kwana uku daurin aure sukace sun fasa, shine shi Alhajin yace na meni shawararka idan ka amince zaka iya auren yarinyar ya baka za'a daura muku aure ranar juma'a inshallah Allahu". Da sauri Mahmud ya dago Yana kallon Malama bakinsa har rawa yake yama kasa furta maganar dazai fad'a Kai ya shiga girgizawa dafa shi Malam din yayi Yana fadin "ka nutsu bazamuyi maka dole ba idan bass sonta sai a nemi wata mafutar" Da kyar ya tattaro nutsuwarsa ya kalli malam yace "Ba haka nake nufi ba, gani nayi yaushe nakai matsayin da za'a bani irin wannan yarinyar aure kamar tafi karfina ni almajiri ne wanda ban aje ba banba wani ajiya ba, kuma tana da ilimi Mai zurfi ba lallai ta yadda ta zauna dani ba". "Ba wannan nake son jiba daga bakinka fadin Kai ko wanene ba taso ba Alhaji shi yafi sanin Kai ko waye amsa muke bukata zaka iya aurenta ko bazaka iya ba ?". Cikin alamar sarewa yace "wane ni ice bana son wannan yarinya na karba na gode Allah ya saka da Alkhairi". Ya fad'a cikin wata irin murya Mai sanyi. "A'a kaje ka nutsu kayi shawara sai ka fad'a min duk huku cin daka yanke, tashi kaje dare ya farayi". Yunkurawa yayi ya tashi Yana fadar "sai da fade" "Allah ya tashe mu lafiya" cewar Malam. Daga falon malam Mahmud bakin titi ya nufa inda yake tunanin ganin Habib Yana son ya karbi lifan dinsa zaije wata unguwa. Gurin Ashiru Mai shayi ya Fara zuwa baya nan sai su salisu da Bashir Suma duk mutanen Mahmud ne hannu ya Basu saka gaisa sannan ya tambayesu Habib wani ne daga can gefe yace "ai yanzu ko runhu ka rike yana gurin Ubaidat kasan mutumin naka Yana neman dauko dala ba gammo". Ya karasa fad'a Yana dariya Bashir ne yace "ko wani Abu ne Naga ko Zama bakayi ba" Da tsaki yayi Yana Dan dafe kujerar kusa dashi Yana fadar "wlh lifan dinsa zan karba zan danje unguwa". "Kai haba saboda lifan kake wannan zagaye zagayen ga nawa kayi amfani dashi mana". Ya fad'a Yana Miko Masa makullin ya karba Yana godiya. Kai tsaye zaranda hotel ya nufa.💋❤️ AUREN HUCE HAUSHI💋❤️ MAMAN FATIMAH. ✨Page two✨ ________📖🖋️ Safa da marwa take tun bayan gama sallar insha'in ta, ta Kira layin wayar tafi sau shurin masaki Amma ta kasa samun Wanda take nema, gumi ne yake fama tsatsato Mata daga goshinta, ta kasa zaune ta kasa tsaye. Gafen gadonta ta koma ta zauna Kara kiran tayi cikin ikon Allah sai Kiran ya shiga da sauri ta nufi kofar toilet dinta na daki ta shige. Bata tsaya amsa sallamar wadda ta Kira din ba ta Fara magana "Asabe me yake faruwa ne tun jiya nake neman wayarki Bata shiga Ina cikin tashin hankali komai fa Yana nema dagulewa, ba alamun nasara a wannan karon tunda komai ya kankama". Shiru tayi tana sauraran wadda ta Kira Asube ta jima tana sauraran ta kafin tayi dariya tace "haba yanzu naji magana da har hankalina ya tashi ki rike sauran maganar sai kin shigo gobe ma karasa". Ta kashe wayar ta bude kofar toilet din ta fito cikin farin ciki da walwala sabanin yanda ta shiga. ___ Mahmud. Ya jima a cikin hotel din kafin ya fito zuwa gurin securities din da alama sun saba sosai Dan yanda suke bashi girma sai abin ya baka mamaki makullin lifan din Wanda ya barwa ya miki Masa tare da fadar "Yallabai an zubo petrol din". Lokaci daya Kuma Yana Miko Masa kudi, kallon na mine yayi masa. "Kudin sunyi yawa ne a sayan man Saida naje na duba maga yawansu". Ya fad'a Cike da ladabi, hannunsa ya zura a aljihun wandon jikinsa ya dauko wasu ya Kara Masa, sannan ya Kuma dauko wasu ya bashi alamar ya baiwa abokan aikinsa. Godiya suka dunga jero Masa Dan inda sabo sun saba da Alkhairinsa. Kai tsaye gurin Ashiru Mai shayin ya nufa duk da dare ya Fara Amma yasan yanzu 'yan term din nasa Basu Isa tafiya gida ba Dan sukan Kai har daya na dare suna hira. Makullin lifan din ya mikawa Bashir Yana fad'a "Jazakumullahu khairan". Habib ne yace "Wai Dan Allah Ina kaje a rufe wayarka tun dazu nake nemanka fa daga inje in dawo kawai na nemeka na rasa sai su Salisu ne sukace kazo nemana ka wuce unguwa". Kusa da Habib din ya zauna na fadin "wash Allah wlh duk na gaji". "Da kayi aikin me". Cewar Habib. "Bari kawai ba aikin da nayi Amma Wanda yake fuskantoni ba sauki kazo muje gida akwai sakonka da Malam ya bani na baka". Ya fad'a Yana kikewa tare da mikawa su Bashir hannu yayi gaba gurin lifan din Habib. Dakinsu Mahmud ya bude daki ne madaidaici da gado guda biyu da wardrobe ta jikin bango sai mirror irin na croom din Nan da AC, kasan dakin shimfide da tayil, lokacin da akazo aikin NGOs din ne aka yiwa Malam nashi falon da Kuma irin wadannan dakunan guda uku sai Kuma dakunan Yara almajirai sama da kasa. Dakin sai kamshi yakeyi, sau da yawa Habib kanshi Yana mamakin wasu abubuwan na Mahmud sai dai ba fuskar da ze tambaye shi duk kuwa da amincin dake tsakaninsu. Saida Mahmud yayi wanka ya saka kayan barci sannan ya Zauna a gefen gadon Yana fuskantar Habib kafin yace. "Kai inaga fa nan da kwana uku zan ankwance". Ya fad'a yana wani killer smile. Zabura Habib yayi ya tashi zaune sosai Yana fadar "Kamar Yaya?" "Kamar yanda na fad'a maka, tsayar Dani da Malam yayi kenan yace Alh Jafar ya bani auren yarinyar Nan da ake bikinta wadda Abdul Hakeem ya kawo Mana IV last week". "Ban Gane ba bafa ta Yaya hakan zata faru?" Kafada ya dage alamun shima Bai Sani ba. "Dan Allah kayi min bayani yanda zan fahimta a sakani a duhu wallahi". "Iya abinda na Sani kenan kawai ance an bani idan inaso inyi shawara". Cikin madaukakin mamaki Habib yace "to Kai ya kace masa?' "Me zance kuwa na karba na gode, kasan har abada ba jayayya tsanina dasu iyayene sak, sun min abinda kowane uba yakewa dansa sun min gata sun Kula Dani lokacin da bana Gane gabas bane Gane yamma bana Gane fari bana Gane Baki, Sun zamar min garkuwar data Hana kowane harbi ya sokeni, Toni kuwa wanen irin butulu ne da zan watsa musu kasa a Ido sufa sun san waye ni Amma suka runtse idonsu suka bani basu nuna min kyama ba, sannan ka dubi yarinyar da aka bani diamond ce fa a cikin gold kasan bani da abinda zan tunkari irin wannan yarinyar da sunan soyayya bare har aje ga maganar aure". Tunda ya fara magana Habib yake Masa kallom mamaki Yana jinjina karfin ikon Allah, lallai wani lamarin sai Allah. Da kyar ya Sami zarafin fadin "Masha Allah! Allah ya Sanya Alkhairi Abu yayi Dadi amma fa ka daina fadar Wai baka da abinda zaka tunkare ta wlh kafin wanna lagwanin Wanda zata aura say millions shi har wani namiji ne kawai Abu daya Sani yana da kudi mu Kuma bamu dasu Amma muna da abinda bashi dashi". "Kamar Yaya me muke da shi Wanda shi bashi dashi? ka duba fa kaga irin yanda yake shiga babban yaro ne ga manyan motoci mu Ina muka gansu" Dan karamin tsaki Habib yayi Yana fadain "ana gabas kana yamma ana maganar nagarta da mutunci da cikar Kamala da siffar mazantaka kana wata maganar, mu an fad'a maka haka zamu dawwama bazamyu arzikin ba". Dariya Mahmud yayi "maida wukar abin Bai Kai haka ba ko Daman haushinsa kakeji ne ban sani ba?" Habib tsayawa yayi galala Yana kallon Mahmud kafin ya karayin wani tsakin "Allah ya sauwake zanji haushinsa Ina ruwana dashi kawai da Daman can no banga dacewar su ba Kai Nifa idan Malam yasa Yara suyi Mata addu'a har cewa nake suyi Mata addu'a Allah ya Bata gwarzon miji na nunawa sa'a". "Amma wallahi Habib baka da mutunci shi wannan ba gwarzo bane?" "Ina fa namiji Yana rausaya kamar mace". "Kaga Yi closing din wanna chapter din yayi zamuyi da wannan lamarin kaga dai komai fa Sai a hankali Dan abinda nake Sami daga wannan organization din ba Isa wannan shidimar zasuyi ba ga yarinyar Mai zafi ni kamar ma tsoronta nakeji fa". Ya fad'a Yana dariya. Sun jima suna tattaunawa yanda zasu bullowa lamarin. _______ Tunda garin Allah ya waye Amma take ta kaiwa da kawowa tsakanin kitchen da dakinta zuwa dakin Baki, Saida aka kammala abincin breakfast aka babba mutane sannan ta samu ta koma daki inda ta samu kanwar Babarta Inna Maimuna a uwar daki. Kallonta tayi "Asma'u ya kamata ki karya kinsan Ina tunanin zuwa anjima gidan ze Fara cika bazaki Sami damar Zama kici wanti abun karki ba, waini ina Hajiya Mama ne Naga yau Bata leko ba?" "Tana bangaren Alhaji Nima nayi wannan tunanin Amma ai lafiya ita keyin shiru". "Hakan ne Kam". Cewar Inna maimuna. ****** Katagum road A dakin Aunty Hasana Zahra ta kwana ita da Autart Haneefa, sai kusan goma ta tashi daga barci wayarta ta Fara dubawa ta tarar da missed calls rababa Amma Sam babu nasa ko na wani daya dangance shi, duk na kawayen da abokanin arziki Bata bi rakansu ba ta shiga toilet wanka tayi, lokacin data fito Sajida ta Samu a dakin ta shigo Mata da breakfast dinta nan, tunda ta fito Sajida ke kallon ta har ta karaso gurin mirror inda sajidar ke zauna murmushi Zahra tayi Mata tana fadin "wannan kallon fa ko na canza Miki ne?". Kai ta gyada Mata "gaskiya Kam ba haka na Saba ganinki ba, meye yake faruwa ne? nifa tun jiya nake nema Deeni da wannan cussing din na Mushahu Aliyu, ta Aliyun tana shiga ba'a dagawa Amma su sauran wayoyinsu switch off". Da rausayar da kanta tayi tana Dan watsa hannuwa "wallahi bani da masaniyar me yake faruwa nima hakan take kamar ke Amma nasan dai kome aje ciki yau dole su shigo garin. Ni wallahi da Aunty Hasana zata yadda da an hakura da wannan mother's day din nifa duk abin ya fice min daga Rai gani nake shima wannan aure ba yuwuwa zaiyi ba nasan dole da wata a kasa ai ba haka muka tsara abubuwan ba Amma kin ko daya fa basuyi attending ba". Ta karasa maganar idanunta na cikowa da hawaye. Hannunta Sajida ta kamo ta rike tana fadar. "Hqba Bestie kada kiyi Kika in Sha Allah ba wani matsala sai Alkhairi kada ki Bata lokacin farin cikinki mana". Aunty Hasana ce ta shigo da sauri alamar wani Abu zata dauka turus tayi tana fadar "ke me zan gani Zahra kukan dai? haba you have to be very strong Mana kada ki yadda aga rauninki a kowane janibi ki Zama jaruma Mai iya fuskantar ko wane kalubale, kada ki kara saka damuwa a zuciyarki zan fita Amma in Sha Allah bazan Dade ba ki shirya kuje sama naji suna cigiyarki". A bangaren Mahmud kuwa bayan anyi sallar Asuba a masallaci ya zauna yayi azkar dinsa Saida gari ya Fara haske sannan ya fito lokacin su Malam sun Gama karatun da sukeyi da maza magidanta. Da sallama ya shiga falon nasa lokacin Abubakar Yana mayar da littatafan mazauninsu, sai da ya zauna sannan ya Dan rankwafa Yana gaishe da malam, Amma sai ya moko Masa hannu sukayi musabiha Yana fadin. "hakan shine sunnar Annabin Rahama Muhammad s.aw.w." Shiru falon ya dauka bayan fitar Abubakar Malam Bai tofa ba haka Mahmud shima, Malam ne ya kauda shirun "Ya ake cikin Mahamuda wace shawara ka yanke?". "Ba damu Baba Malam na karba na gode ayi min godiya Allah yasa hakan yafi Alkhairi". "Allahumma Amin. Allah ya Sanya Alkhairi ya Baku zuri'a Mai Albarka Allah yasa ace gara da akayi hakan" A zuciyarsa yake ta amsawa da Amin. Harya yunkura zai tashi Malam yace "koma ka zauna, Ina zaka bamuyi maganar inda zaka ajeta ba da sauran shirye-shirye". Sadda Kai yayi haka Nan yaji wani irin nauyin malam din ya taso Masa. Kansa Yana kallon kasa yace "so nake muyi shawara dasu Habib yanda muka yanke saiya fad'a maka". "A'a ba haka za'ayi ba nizan bada sadaki da kayan goro da alewa sai Kuma shaddoji da za'a kawo an jima Suma dinkakkune tunda abun yazo a kurace, sai Kuma gidan Nan na Hayin Banki mukullin na gurin Binya tun jiya na bashi nace yau zakuje a duba abinda za'ayi Masa". Mahmud kasa magana yayi shi wannan gatan har yayi Masa yawa komai anyi Masa. Rarrafawa yayi kamar yaro har gaban Baba Malam ya rinka godiya har Saida yayi Masa fad'a. ******** Amma ce da Inna a uwar dakin Ammar bayan dawowar Ammar daga bangaren Alhaji cikin tashin hankali Innar ta kalli Ammar tana fadin ke Asama'u wace irin magana ce wannan yaushe hakan ta faru duk bamu da masaniya?" Dan nisawa Ammar tayi. "Wallahi Nima ban sani ba Amma yace kada yaji kada ya gani naja bakina nayi shiru yana zargin kowaye yake lalata lamarin auren yarinyar Nan na kusa yake tunda yace min Malam Bukar ne yayi binciken Dan haka bazai cewa kowa komai ba har sai bayan daura auren tukunna". "Ya fad'a Miki waye mijin?" Kai ta girgaiza Mata alamar A'a. Nifa Ina gudun garin AUREN HUCE HAUSHI a kwaso bara gurbi Wanda za'azo ana Mana dariya". "Gaskiya bana tunanin haka Inna mu bita da addu'a kawai Allah ya Zama gatanta yasa albarka a ciki. 💋❤️ AUREN HUCE HAUSHI💋❤️ Story & written By ✨MAMAN FATIMAH.✨ INA MIQA SAKON TA'AZIYYATA GA 'YAN UWANA HAJIYA MARIYA ALIYU ( JIMMAN ADO) HAJIYA BILKISU ALIYU (UMMA IKKI) HABIBA ALIYU (UMMA HABIBA) Na rasuwar mahaifinsu ALHAJI ALI DAN HAYA MAGAMA KAZAURE. Allah ya jikansa ya jaddadda Rahama a gareshi tare da sauran musulmi. Page three 🔷 📖🖋️ .............. Tunda Mahmud ya fito daga gurin Baba Malam yake nazarin yanda zai bullowa lamarin, baya son ko kadan a Sami kurkure, guri ya Sami nesa da makarantar kasancewar Alhamis ce Yara basa karatun safe sai ya zamana yawancin su suna dakunan su. Waya ya Ciro daga aljihun wandonsa yayi dialing din number Bata jima tana ringing ba kada daga magana ya Fara "kana jina Sameer sakon Dana turo maka kada a samu kuskure kayi kokarin ganin komai yayi yanda ya kamata fa". Dan Jim yayi alamun ana fad'a Masa wani abu "Ok to shi kenan take care". Ya kashe wayar. __ Nama ne da kayan miya ake ta shigo dasu cikin gidan da manyan kuloli sabbi Hajiya mama ce a kofar kitchen din na tsakar gida tana bada umarnin abinda za'ayi, yaran dake shigo da kayan ta kalla "wannan fa daga Ina?". Magaji ne ya Bata amsa kafin yaron data tambaya ya fad'a Mata "tare muke Mama na abincin bakin Abba ne". "Ikon Allah Naga ai an kawo wasu da sassafe dazu gasu nan har an kusa Gama aikinsu". "Eh to shi dai yace a kawo wadannan ma". Magajin ya fad'a Yana shiga dakin Amma. "Kai dawa Kuma kake tafiya kana magana" Cewar Inna maimuna. Kusa da ita ya zauna Yana fadin "nida Hajiya mama ne kayan miya ne da Naman rago Dana kaji Abba ya Kara badawa aka kawo shine take magana ko yayi yawa kame?" Dan murmushi Amma tayi "Abban Nan naku baya son a zauna lafiya wallahi magaji kamar zai aurar da Yara uku sai irin wannan shidima yake haka". Kai magajin ya jinjina "Amma kenan kin manta yanda Abba keson Zahra ai kawai kowa ya zuba Ido ana auren uwar masu gida tab ai kowa sai yasan anayi Yasin, ki Bari kawai Ammah Nan zan kawo nama a ajiye min". Ya fad'a Yana dariya ya nufi kofar fita saboda sallamar wasu Mata da yaji a kofar dakin. ___ Daki Mahmud ya koma ya samu Habib a tsaye a tsakar dakin da alama daga wanka ya fito, saida ya Gama wayar sannan ya kalli Mahmud. "Wai ina kaje ne? Naga fitowarka daga gurin Baba Malam kafin na saka caji na nemeka na rasa, Bilya ne ya kirani Wai mu sameshi a hayin Banki shi Yana can yaje da masu aiki su duba yanda za'ayi gyaran" Dan Dafe Kai Mahmud yayi ya Dan fesar da numfashi. "Ikon Allah Wai Daman kamar jira kuke ace za'ayi min auren Nan kowa sai rawar jiki yake yi, daga fad'a shine har ya want kwashi jiki da masu aiki ya tafi tun garin Bai Gama watstsakewa ba". "Naka wasa ne Alaji, aini yanzu haka mun Gama magana dasu Bashir sunce mun gasu Nan zuwa har suna cewa shegen zurfin ciki ne da Kai baka fad'a musu ba jiya ko kunya kakeji irin ta Mata". Ya karasa maganar Yana dariya. Har ya nufi gurin mirror ya tsaya "kaji na manta ba Salis yace na tura Masa cikakken sunan da ze saka a IV da zeyi a waya ya turawa friends na kusa". "Ok ba matsala ka tura Masa kawai da sunan aika Sani ba saina maimaita make ba". Misalin karfe Sha daya na safe wata bakar Hilux sabuwa kar ta dira a kofar gidan Malam Bukar. Lokacin yaran sun firfito suna sugogin su masu wanki nayi masu wasa nayi Amma idan ba fada maka akayi bazaka taba cewa yaran Almajirai bane kowa cikin tsabta Kuma a lokacin anyi hutun makarantar book shi yasa basayi tunda suma tsarin makarantar gwamnati suke bi. Mutane biyu be suka fito daga motar da sauri 'yan samarin dake kusa taso da sauri suna fadin barkan ki da zuwa kasancewar sun saba dasu sosai sune wadanda suke kawo musu tallafi daga organization din. Da sauri suka bude musu falon saukar bakin Malam kafin wani ya shiga ya fadawa Malam din. Ba jimawa Malam din ya fito suka gaisa a mutunce, sannan suka gabarwa da kayan abincin da suka kawo sannan suka gabatar Masa da bukatar daukar Mahmud zuwa wani taron karawa juna Sani na makarantun tsangaya Wanda za'ayi a kano, tunda shine Wanda suka dauka aiki a Nan tsangayar yake wakiltar su kuma gobe juma'a za'ayi taron na Rana daya ne kawai. Dan Jim malam din yayi kafin yace " Ikon Allah malam Sameeru ga koshi ga kwanan yunwa WALLAHI shi Mahmudan dai baze Sami damar halartar taron nan naku ba, domin a goben in Sha Allah za'a daura Masa Aure". Cikin wani irin madaukakin mamaki Sameer dake kusa da Malam din Kuma jagaban tafiyar ya kalli Malam Yana cewa. "Aure! Kuma Malam?". Kai ya jinjina Masa alamar tabbatarwa, "yanzu haka suna can gidan da ze zauna ana dudduba gyaran da za'a Masa duk da gidan Bai jima da kammaluwa ba kasan kullum abin duniya sabuntashi akeyi". Kai ya jinjina ya hadiye wani yawu da kyar shifa duk ya shiga rudu meye hakan Wai Kuma. Fara'ar dole Sameer ya kirkiro Yana kallon Malam yana fadar "Masha Allah Abu yayi Dadi to ai mu wannan lamarin namu ne munzo a dai dai kenan tunda Abu ne na ma'aikacin mu koma kunya zatayi Masa malam kada kuyi komai yanzu zanyi waya za'ayi duk abinda ya kamata tun daga abinda ango ze saka har abinda za'aci duk Yana karkashin kularmu tunda mu yakewa aiki, Kuma zamu zauna sai an daura auren damu in Sha Allah. Maganar taron Kuma sai dai a daga zuwa wani lokacin Dan bamaso wani yayi missing gaskiya". Tunda Sameer ya Fara Kora bayani malam ke jinjina Kai saida yake Aya sannan ya Sami zarafin magana. "To malam sameeru anyi haka abin fa da yawa kids bakuzo da Shirin wannan abun ba kunzo Kuma kuyi ya kuyi makarbiya ai da wahala abun". Dariya Sameer din yayi Yana fadar "malam ba abunda ze gagara kungiyoyin masu karfi ne, yanzu ma ga wannan saboda biyan sadaki". Ya aje Masa cheque na Banki suka Mike Yana fadar "Bari na Nemo shi a waya sai muje muji meye shirye-shiryen nasu, a huta lfy". Suka kad'a suka fita. _____ Kyakykyawan guri ne Aunty Hasana ta kama inda za'ayi mother's day din gurin ya kayatu ba karya kudi dai an kashe su gurin Kama event center din, anyi taron Mata 'yan gayu kamar ba gobe amarya tasha kyau kamar a dauke ba boye. Ga wani slow music da mc din ya saka na wakar Amarya da ango kowa ka gani cikin nishadi yake sabanin Amarya da Yayarta Banda ta Riga ta gayyato mutane harda wadanda sukayo Mata tafiyayya sukazo da ba abinda ze saka tayi wannan taron to Amma mutum Bai Tara Sani ga Allah ba. An raba kayayyaki na alfarma na bikin, sai magariba taron ya tashi, zuwa yanzu 'yan Qananan maganganu sun Fara fita a tsakanin kawayen Zahra tunda har zuwa lokacin ba wani duriyar Ango ko wani nasa, sai Dan kus-kus ake abinda yafi bada mamaki bai wuce ganin anata faman programs ba normal. Su Mahmud Basu samu kansu ban sai bayan sallar insha'i lokacin suka zauna Dan wuni guda suna ta faman sunturi daga can zuwa can abin dai ba sauki dan su sameer suna zuwa gidan suka babbago aikin da sai anyi sati ba'a Gama ba Dan sunce tsarin gidan gaba daya za'a sake, basunda ta cewa tunda oganninsu ne sai godiya suka dunga zubawa harda su Bashir. Gurin karfe goma malam ya Kira Mahmud a waya yace yazo cikin gida ya same shi. Saida ya leka falon iya Abu suka gaisa tana faman jansa tana ita ce ta karfen Dan haka ita zata koma sabon gidan a kawo Amarya nan. Da haka ya karasa turakar malam Yana zaune a falo Yana sauraren wa'azi a TV, yayi sallama Malam din ya bashi izinin shiga, Nan kasa ya zauna Yana gaishe da malam din.Wasu manyan ledoji malam din ya nunawa Mahmd Yana fadin. "Dauko wadan can kayan ka duba daya Wanda nasa a kawo maka ne biyun Kuma wadannan masu kungiyar ne ta taimakon tsangayu suka kawo ga lemuka can da ruwan roba sun kawo yafi catoon dari sunce kada ayi abinci ma duk za'a kawo, har na rasa da wane bakin zan gode musu, sai dai Ina rokon Ubangiji s.w.w yafi mu yabawa, naji su Habibu ma sun ce sun dauko aiki Mai yawa a wancan gidan ko?" "Eh wallahi munyi-munyi su Bari suka Kiya Wai haka aikin Qungiyar yake in dai kana musu aiki idan wani Abu ya sameka Mai Dadi ko marar dadi su zasu tsaya maka". "Alhaji yace min kun shiga dazu bayan sallar magariba har da bakin kunyi Masa godiya, kun kyauta haka ake so". Lokacin Mahmud ya koma dakinsu Habib baya Nan gurin da yake aje makullin lifan dinsa ya duba ya kuwa you sa'a yana nan, lodojin ya zube a kan gado ya dauki makullin ya rufe dakin ya hau mashin din yayi gaba. Bai dawo ba sai kusan Sha biyu da rabi har lokacin kuma Habib baya dakin yasan suna can suna kujuba kujuba. Yauma Zahra taso kwana a dakin Aunty Hasana saboda tana bukatar kadaicewa Amma Sajida ta matsa Mata da mita Saida suka tafi Amma fa zuciyarta Bata da nutsuwa gashi tana ankare da Aunty Hasana tun jiya da dare a taje can gida cikin gari Bata da nutsuwa ko alama Amma tana ta kokarin ta basar sai dai ko Yaya mutum ya shiga damuwa indai kayi Masa farin Sani zaka fahimta, ita Abu mafi Bata mamaki yanda aketa kwaramniyar bikin ba wani canji sai dai abunda baza'a rasa ba duk da Daman ba wata muguwar bidi'a ba ta had'a, walima ce kawai Bata Sami ba saboda tace ita malam Tijjani Ahmad zeyi Mata Kuma bayanan yana Umara. Tunda tayi sallah ta kasa tashi daga gurin tana kallon su Sajida sunata sabgarsu, Amma ita da wata irin faduwar gaba ta tashi ta rasa nutsuwarta kwata kwata da kyar ta tsahi sauko kasa gurin Aunty Hasana a fall ta sameta tana hadawa Abbansu Haidar break fast. Gurin dining din ta karasa tana gaishe shi sannan gaida Auntyn. Dakin Auntyn ta shiga kwanciya tayi tana ta faman sakawa da kwancewa zuwa yanzu dai tasan tabbas da matsala sai dai yanda ba Wanda ya fad'a Mata shi yasa itama ta zubawa sarautar Allah Ido taga iya karshen film din tasan ko menene yau dai za'a yita ta Kare tunda yau ne deadline duk wata kunbiya kunbiya za'a zazzageta. Tun karfe goma Mai yiwa Amarya make up tazo Amma kememe Zahra tace ita bataso a kyaleta aka dunga yiwa kawayenta, ganin guri ze kure ne Sajida take ta fadawa Aunty Hasana Saida tazo sannan akayi Mata light makeup Amma fa duk da hakan tayi karshen kyau, farin material ne ta sakata Mai touching din sky blue sai aka daura Mata head shima sky blue din takalman da pos din duk sky blue din ne. Wani san sanyan kyau tayi na ban mamaki, komai na Zahra Mai kyau lallai zaharar ce Dan duk cikin kawayen Bata da mahad'i. A babban masallacin juma'a za'a daura auren Masha Allah, ango ya fito Shar abokansa sai mamakinsa suke Basu taba sanin kyawunsa da cikar haibarsa ya Kai haka ba sai daya fito sun Sha mamakin kwarai har wasu suka Fara kokonto a kansa, Yana kallon yanda idanun sukayi Masa caa. Dan dakakkiyar getzener ta saka ga takalman da agogo ga hula, Sam bazaka taba cewa Wai alamajirin malam bane ba, ga wani irin kamshin tunda ta tumkaro taron abokanensa kamshin ya hade gurin. Daga gefe sameer ne da abokinsa Naraddeen suna tsaye lokacin da Mahmud ya fito Sameer ya kalli Naraddeen din yace "wallahi wannan guy kwallon Dan duniya ne na rasa Gane kan alkiblar daya kalla Wai aure zai daura shi kadai kamar marara gata, ni so nake Naga karshen wannan wasan kwaikwayon nasa. Daga inda yake tsaye ya kafe Sameer da Ido ko Bai fad'a ba yasan me yake nufi tun jiya yake tuhumarsa aka zuwa da abokinsa da yayi duk da ya nuna Masa wannan ba wata matsala bace Amma har yanzu Yana hukunta shida idanunsa. Masha Allah dubban mutane ne suka shaida daurin Auren FATIMAH ZAHRA AHMAD SANI da Angonta MAHMUD MUHAMMAD DANGE akan sadaki dubu dari uku lakadan ba ajalan ba. Daurin aure daya bawa dubun mutane mamaki bare wadanda sukazo daga bangaren Mushahu sunyi mamaki kwarai sunan Amarya dai shine Amma ba mijin daya gayyato su bane yayin da yan unguwa ya Zama abin kasawa a faifai ana yawo dashi, da yawa na ganin beken Alhaji Jafar na aurawa bakon da ba'asan asalinsa ba yarinya kamar Zahra yayin da wasu ke fadar ai Dan ba 'yarsa bace shi yasa yayin wannan danyan aikin. ....... 💋❤️AUREN HUCE HAUSHI 💋❤️ Page four🔷 ___________''📖🖋️ Wata marokiya ce irin dattawan Nan da suke bin manyan marok'a ta biyo tawagar masu dawowa zuwa gida kasancewar gidan ba nisa daga masallacin juma'ar, itace ta rangad'a guda har sau uku ta Kara da fadin "Alkawarin Allah ya tabbata an daura auren Fatima Zahara'u da zukeken Angonta Mahmud Ubangiji Allah ya bada zaman lafiya da kazantar daki Bata shara ba, munzo much arziki mubar arziki a gurinsa. Kamar saukar aradu haka maganar ta shiga kunnen Hajiya mama, batasan lokacin data tsallake mutanen falonta ta fito ba dankwalinta a hannu, tana fadin "me naji ana fad'a wa aka daurawa aure da Mahmud naji kowa". "Eh haka ne Kam Alkawarin Allah ya ciki Zahara'u ta Zama matar Mahamuda" Ta debo wata gudar ta Kara rabsawa. Dai dai lokacin Hajiya kaltume aminiyar Ammah ta fito ta dukulawa wannan marokiyar kudi sannan ta Mika Mata babbar leda Mai abincin biki har da ruwa da lemo. Cikin rashin nutsuwa Hajiya mama ta nufi dakin Amma ko sallama Babu ta Fara fadar "Hajiya kinji abinda naji ko kunnena ne ya jiyo min ba dai dai ba?". Kallonta duk 'yan dakin suke kafin Ammar tace Mata "nima haka naji kamar yanda kikaji sai dai ko shirme takeyi ita Mai rokon tunda ba sanin su tayi ba". "Eh gaskiya Kam sai dai hakan". Ta juya ta koma daki. Bata zauna a falon ba uwar daki ta wuce, Asabe ce ta rufa Mata baya, a tsaye ta sameta ta Goya hannu a baya tana Dan Kai kawo a tsakanin gado da madubi. Waiwayowa tayi tana kallon Asaben kafin ta zauna a bakin gado, kusa da ita Asaben itama ta zauna. Tana fadar "Haba Hajiya Dan Allah ki nutsu bana son ki bada wata baraka a sabgar Nan keda na fad'a Miki Daman malam na BANDE yace wannan karon aure sai anyi Amma ba da Mushahun ba, Amma abinda yake daure min Kai malam na banden yace Wanda zata aura a nesa yake Kuma yaga haske so sai akan lamarin duk yanda yaso ya Bata lamarin abin Bai yuwu ba shine nace kawai a kyale tunda dai Wanda muke son a fasa da shin din aikin ya yuwu, nasan dai da wuya ta Sami irin Wanda ta rasa a bay". "Haka ne Amma abin dubawar waye wannan din sanan me yasa aka kudundune zance? Wai fa Dan munafurci Hajiya Asma'u cewa tayi Bata Sani ba ke kin yarda Alhaji ze aurar da Zahra Bata da masaniya, ko meye ma dai kyawaun ya kare a auren Hadi tunda nasan ba wani sai Mushahun shi Kuma ya Kara gaba kamar sauran". Ta fad'a tana kwafa, mikewa tayi tana gafar "Bari na fita sai Naga kul uwar daka". "Allah ya taimaki uwar dakina, aikinki Yana kyau". Asabe ta fad'a tana mikewa itama. ********** Daga gurin daurin aure Kai tsaye gidan gonar Alhaji Jafar suka wuce har tawagar angon bisa umarnin Alhajin tun safe ya turo Mai sunasa (magaji) yaje ya fadawa Baba malam. Anci an Sha kamar ba gobe mutane sunyi mamakin irin wannan karamar arzikin dan duk zarin mutum sai dai yaci ya Bari ruwa da lemo kuwa kamar banza. Abokan Mahmud kuwa sai Dan biki suke Masa. A gidan malam ma Masha Allah anci an Sha Yara sun san ana biki a gidansu, Iya Abu ma tayi nata taron komai baja baja makotanta ma sunsan ana hidimar arzki a gidan Kuma Suma sunzo Mata harda masu riko abin arzikinsu su kawo Mata. ******** A guje Faruq ya Fado falon Aunty Hasana,danta ne na uku Yana rungume da babbar rigarsa ta daurin aure daya saka Yana Fadi "Aunty Zahra wallahi Naga mijinki ba wannan Uncle din bane na kano wallahi wanna yafi shi kyau Baki gani ba yanda yake rabawa marok'a kudi ba, Kuma Dan gayu ne sosai Naga Uncle Abdul Hakeem ma ya rugume shi Yana ta dariya, Dana tambayi Auncle Imam yace min sunansa uncle Mahmud". Tunda ya shigo Yana karadin Nan ta zuba masa Ido tana sauraren abinda yake fad'a, kana ganinsa kasan har zuciyarsa abinda yake fad'a din gaskiya ne, wani irin gingirin taji kanta yayi mata, nan ta sulale ta kwanta kan kujerar ta saka hannunta ta rufe fuskarta wasu hawaye na zubo Mata masu zafi. Sajida da Amatu suka nufi gurin Faruq din suna neman Karin bayani. Yayin da wasu da yawa suke ta sabgar ciye ciyensu Dan Suma Kam an kawo koma enough. Kamar yanda ya fad'a haka Suma ya mayar musu Dan su harda Karin bayanin yayi musu kasancewarsa Mai surutun tsiya. A hankali Sajida ta kamo hannun Zahra Dan Bata fatan wani daga cikin bakinsu su fuskanci an samu matsala gaskiya, kamar masu you shawara suka shiga dakin Auntyn saboda Nan ne baza'a shigo ba. Bakin gadon ta zaunar da Zahra ita Kuma ta janyo stool ta zauna har lokacin Bata saki hannunta ba,tana Jin yanda ilahirin jikinta yake rawa. Hannun ta Kara jimkewa cikin nata tana fadar. "Cool down Mana bestie haba take it easy, kada ki tada hankalinki Taya Zaki kama maganar faruq kinsan dai ba wani hankali ya Gama Masa jiki ba". Kai ta shiga girgizawa cikin muryar Kuka tace. "Wallahi Saji akwai matsala kema Kuma kin sani sai dai kik'i fad'a idan ba matsala Ina su Maryam da mukayi dasu zasu zo tun kwana ukunda suka wuce Ina shi kanshi uban gayyar ina su Deeni dasu Aliyu, kowa ka Kira sai dai kaji switch off baka haka ba". Ta fad'a tana fashewa da wani irin Kika.mai taba zuciya. "Kiyi shiru Dan Allah kada ki janyo hankalin mutane Mana kinga ga Amatu can zataji dasu ki nutsu har muji meye gaskiyar maganar Mana". "Ki barni nayi kuka wallahi na gaji nikenan kullum matsala daga wannan sai waccan na rasa a Ina matsalar take ni wallahi bana son kowa ma a kyakeni haka Nan bana son auren, bana so wallahi ni nagaji Allah Jordan zan tafi bazan zauna ba, bazan Kara Zama a kasar nan ba". Ta fusge hannunta daga na Sajida ta yunkura ta tashi ita dai Sajida Bata San ta Yaya akayi ba sai ganin Zahra tayi ta kifa kan gadon tana wata irin fuzga da gudu ta karasa kusa da ita tana jijjigata tana fashewa da kuka tana fadin "ki tashi Dan Allah wayyo Allah na". Baba Tabawa ce ta bude kofar ta shigo, Dan tunda tana kusa dasu Faruq ya shigo da wannan maganar duk da tasani Dan Aunty Hasana Bata rufe Mata komai ba ta fad'a Mata tun jiya, shi yasa data ga sun nufo dakin hankalinta ya kasa kwanciya ta biyo su tasan koya Sajida zatayi Mata kalamai ba kamar ita ba tunda abinda babba ya hango yaro koya hau iccen rimi bazai gano ba. Turus tayi tana kallon Sajida dake Kuka bil hakki tan jijjiga Zahrar. Da sauri ta karaso tana fadar "ke 'yan Nan menene haka?". Hawaye jage-jage Sajida ta dago tana fadar "wlh Baba Tabawa kawai tana kuka tana maganganu tana tashi kawai sai Naga ta yanke jiki ta Fadi?. Wani ruwa Baba Tabawar ta dauko a kan bedside fregde din Nan ta zubawa Zahrar a fuska Amma shiru ta Kara watsa Mata Nan ma shiru cikin tashin hankali ta lalubo Yar wayarta rakani toilet ta mikawa Sajida "ungo maza Kira min Aunty zakiga an saka Maman Ali yi sauri". Bugu biyu Auntyn ta dauka tare da sallama, gani Sajida ta rasa me zatace ne yasa ta mikawa Baba Tabawa wayar. Can Kuma tana ta faman" hello Baba" Abinda taji kenan lokacin data Kara wayar a kunne cikin sauri Baba tace "yi sauri ki turo a Kai Zahara'u asibiti wallahi gata Nan a suma min yayyafa ruwa a banza". Bata jira taji me za'a fad'a ba ta kashe wayar. Abdul Hakeem Aunty Hasana ta lalubo a waya lokacin suna tsaye shi da Mahmud suna magana wayar Abdul Hakeem dince ta Fara ringing Sunan Aunty Hasana ya gani ya daga har zai Fara Mata abunda ya saba ta tsayar dashi tana fadin "Dan Allah maza kaje gidana ka dauko Zahra ku wuce asibiti mu hadu a can wai Suma tayi" Kit ta kashe wayar. "Innalillahi wa Inna ilaihi raji'un yake ta Nanatawa da sauri Mahmud ya tambaye shi "lafiya meya faru". "Bari kawai ba komai Ina zuwa yayi gaba da sauri jikinsa har rawa yake Yana tafe Yana laluben key din motarsa. Da sauri Mahmud ya biyo bayansa' Sam baiji key din ba sai daga baya ya tuna tana hannun mustapha yaje gari ya dawo. Tsaki yayi daidai lokaci da Mahmud din ya karaso Yana fadar"Dan Allah Wai menene Naga duk a rude". "Bari kawai Wai Zahra ce ba lfy zan kaita ASIBITI". Kallon yayiwa Abdul Hakeem din kafin yace "shine Kuma zakaqi fad'a min". Hannu yasa ya yafito Sameer, cikin bada umarni yace "Dauko motar can kuje da Abdul zaku Kai madam asibiti". Ya juya ya koma gurin su Habib. Har sukaje gidan Auntyn Abdul Hakeem Bai daina mamakin Mahmud ba, yanayin yanda yayi maganar kawai kasan da abinda ya taka umarni fa ya bada, su dai a zahiri ai Sameer ne uban gidan Mahmud tunda kowa yasan aikin NGO's ya kawo shi garin har suka hadu da Mahmud din suka dauke shi yake musu aiki a sauran makarantun tsangayun na cikin gari Dana kauye. Da sauri Abdul Hakeem din shiga gidan Auntyn ta kofar baya gurin kitchen ya shiga koridon dakunan barcinta. A tsaye cirko cirko ya samu su Baba Tabawar har lokacin numfashinta Bai dawo ba. Da sauri ya karasa gaban gadon yasa hannu ya dauketa kamar wata Baby yayi waje da ita. Sajida da Baba Suka rufa Masa baya. Da sauri Sameer ya bude Masa seat din baya ya sakata Sajida ta shiga ita da Baba shima Abdul Hakeem ya shiga gaba da gudu Sameer ya fizgi motar. Saida ya daidaita a titin sannan ya kalli Abdul Hakeem din "ina muka nufa?". "F.M.C zamuje tunda yafi kusa". Nan da Nan aba karbeta likitoci suka rufu a kanta, suna Nan tsaye Aunty Hasana tazo ita da Inna maimuna sai Hajiya kaltume. Suma tsayawa sukayi a gurin Baba Tabawa tana maida musu yanda akayi ita dai Sajida ba baka sai sharar hawaye take. Su Abdul Hakeem suna suna gefe daga zuwansu Mahmud ya Kira akai sau biyar idan ya Kira Sameer sai ya Kira Abdul Hakeem, daga Jon yanayinsa kasan Yana cikin damuwa abinda ya Kara daure Abdul Hakeem Kai yandq Sameer yake amsa wayar Mahmud cikin kulawa da bada girma. Sun dauki a kalla minti arba'in kafin babban likitan ya fito sannan sauran Suma suka fito. Su Abdul Hakeem sun bin bayan likitan kamar yanda ya bukata Amma ganin an gungoro Zahrar a gadon daukar marasa lafiya yasa suka nufe ta da sauri suda su Aunty Hasana. Wanda ya turo gadon ne yace "ai ta farfado ba wata matsala ana so ne dai ta samu hutu sosai jininta ne yaso Hawa Amma cikin ikon Allah anyi controlling dinsa". "Oh no 'yasu Allah ka dubi lamarin wannan 'yar maraiya duk da Bata tashi da rashin gata ba sai yanzu ka kawo Mata Tata jarabawar Allah ka shiga cikin lamarinta". Aunty Hasana ta fad'a itama tana goge hawaye. Baba Tabawa dasu Sajida suka amsa da "ameen ya Rabbi" Dakin 'yan da'i da'a aka kaita tunda tana bukatar isolation. Saida komai ya Zama dai dai an saka Mata drip sannansu Sameer sukaje gurin likitan. Fad'a yayi so sai akan yanda akayi har karamar yarinya kamar wannan damuwa tayi Mata yawa har har take barazana ga lafiyar ta. A can gidan biki Kuma Amma ta rasa inda su Hasana da Inna suka tafi Dan hankalinta Bai kawo Mata Hajiya kaltume ma Bata Nan ba sai da abokiyar zamanta tazo sannna ta fuskanci itama Bata Nan din wayarta ta dauko ta Kira Hasana, lokacin tana zaune gaban gadon da aka kwantar da Zahrar. Sunan Ammah ta gani sai lokacin ta tuna Ashe Bata fad'a Mata ba. " Assalamu Alaikum Ammah". "Wa'alaiki Salam warahamatullahi ta'ala wabarakatuhu, wai Ina Kika tafi ne babu ke Inna maimuna ma Bata Nan Hajiya kaltume ma banganta ba". Dan Jim tayi har Saida Ammah tace "kina jina?" "Eh inaji Ammah duk muna tare dasu, muna Nan gurin Zahra Bata Jin dadi ne Amman da sauki yan haka barci take". "Wane irin zance ne wannan kamar Bata Jin dadi Kinga Hasana fadi min gaskiya yanzu kina Ina?". " Muna F.M.C wlh jikin da sauki sosai kawai sunce ana dai San ta huta ne, kada ki tada hankalin Dan Allah". "To Allah ya kyau Amma Ina hankali ze kwanta". Waje Aunty Hasanar ta fito gurin su Baba tabawa da sajida tace "Baba tabawa Dan Allah kuje gida da sajida tasan inda aka aje abubuwan da zasu bawa kawayensu tunda yau zasu wuce sai ki fad'a musu tana gida gurin Abba, ta kalli Sajida ke Kuma duk tmbayar da saying Miki kice Baki Sani ba mu barsu a haka". Kudi ta mikawa Baba tabawan sannan ta karasa gurinsu Inna maimuna da Hajiya kaltume, Suma bayi tayi musu na Kiran Ammah tace suje gidan Dan hankalinta ya kwanta. ********* Da kyar Amma ta Bari akayi sallar magariba ta shiga bangaren Alhaji Jafar ta same shi da Hassan da Abdul Hakeem suna magana akan Zahra Hassan Yana ta mitar meyasa Abban yayi haka ai da hakuri kawai akayi har lokacin da Allah ze kawo Mata wani. Dan murmushinsu na manya yayi Yana "fadin wannan ma in Sha Allah Babu Dana Sani a cikinsa ni nasan nagartar Dana gani tare da yaron yasa na bashi, Kuma ko bayan Raina zakuce na fad'a muku". Jiki ba kwari Amma ta gaishe da Alhajin tana Masa ban gajiya tare da godiya. Sannan ta Dora da fadin "Dan Allah ko zaka Bari naje Naga jikin nata?" Tsai yayi Yana kallon ta "da kinyi hakurin zuwa Suma da anjima zasu taho gida yanzu ma daga cen muke ko zuwan mu Bai isar ba?" Cikin Jin nauyinsa tace "A'a ya badatar" Ta tashi ta nufi kofa da kallo Abban ya bita ita kanta tausayi take sashi da gani zuciyar ta ba Dadi. Da sallama suka shiga dakin lokacin Aunty Hasana tana sallar insha'i ita Kuma zahra farkawarta kenan tana kokarin tantance Wai inane ma Nan din inda ta gani idan dai ba gizo idanunta ke Mata ba kamar asibiti. Sallamar ce ta katse Mata tunani ta Dan dago kanta kadan sukayi arba dashi Ido cikin Ido da sauri ta runtse idanunta zuciyar ta na wata irin bugawa tana ambaton Allah a zuciyar ta, meya kawo wannan dodon nata gurinta, Kara rufe idanun tayi it fa wallahi zata iya rantsewa Allah duk duniya ba idanun da suke figitata kamar nasa. 💋❤️ AUREN HUCE HAUSHI 💋❤️ Strory & Written By MAMAN FATIMAH Page five 📖🖋️ _______ Shiru dakin ya dauka har zawan lokacin da Aunty Hasana ta idar da sallar. Dan juyowa tayi kadan tana fadin "wa'alaikumus Salam warahamatullahi ta'ala wabarakatuhu, sannunku da zuwa Bismillah ga kujeru nan ku zauna". "To mun gode Aunty" Sameer ya fada. Cikin ladabi da mutuntawa suka gaishe ta tare da tambayar Mai jikin, ta amsa musu da sauki, sai kuma dakin ya Kara daukar shuru Zahra dai tunda ta rufe ido Bata Kara gigin budewa ba, ita ji take duk ya cika dakin ita tun ganinta na farko dashi a duniya ya birkita Mata lissafi, Kuma saboda Allah meya kawo shi gurinta asibiti duk da tasan mutumin Ya Abdul Hakeem ne Amma sai taga kamar ba sai yayi Masa Kara ba, ko Kuma yazo wata sagbar ne asibitni ya Sami labarin shine ya shigo ya dubata. Magaji ne ya shigo dakin da sallama sai Kuma ya Dan tsaya baiyi tunanin ganinsa ba Sam da fara'a ya karaso Yana fadin "Ashe Kuna Nan ai tare muke da Ya Abdul Hakeem ma". "Ok" abinda Mahmud ya fad'a kenan Shi Kuma Magajin ya karasa gurin Auntyn Yana gaishe ta. Abdul Hakeem ne ya shigo Yana rike da wayarsa a hannu da sauri ya karasa gurinsu Mahmud din Yana fadin "A'a angon ne da kansa" Yana Mika masa hannu. Saroro Aunty Hasana tayi ita wace iri ce kawai dai taga sun shigo sun gaisa wallahi Sam Bata kawo ba ita da akace Mata Alamajirin Baba malam ne ai ta dauka irin wannan gaddawan ne, yo ta Ina wadannan sukayi wani Kama da kolaye ai ita zallar ilimi ta gano da wayewa a tattare dasu. Hanyar wajen ta nufa tana janye da hannun magaji duk sai taji kunya ta kamata Ashe sukanta ne. Ita kuwa Mai gayya Mai aikin ai tana jin an ambaci ango ta bude idonta girjinta Yana wata irin dokawa "ango a nan to waye a tsakaninsu da suka shigo tare? Abdul Hakeem ne ya kalli gurin gadon Yana fadi. "Masha Allah! Ashe kin tashi, ya jikin?" Ya fad'a Yana karasawa jikin garon Sameer ma Dan matsawa yayi Yana dubata Kai kawai ta gyada musu, tana kallon Ya Abdul Hakeem din, kallo irin na neman Karin bayani. Yi yayi kamar Bai Gane ba ya juya yana yiwa Sameer magana suka fita. Har suka fice Bai dago ba Yana ta faman tab'a waya sai da ya Mula Dan kan shi sannan ya tashi ya tunkari gadon. "Ya jikin?" Ya fad'a Kai tsaye, Bai Kuma jira ta amsa ba Dan ko kwakwkwaran motsi ta kasa sai tunanin da yake Mata Kai komo. "Badai wannan bane ake nufin an daura min auren dashi Amman da Naga ta kaina". Shine ya katse tunaninta. "Ki kwantar da hankalinki ki daina saka damuwa a ranki da kannan shekarunki, ki kuma dagawa Ammah í nata hankalin, idan nine bakya so ba damuwa Nima kusan hakan take. Amma kada mu watsawa iyayen mu kasa a ido Mana tun yanzu gara ki nutsu ki kwantar da hankalinki daga baya sai a duba Mai yuwuwa tunda nasan bazaki so Zama da almajiri marar karatun boko mai zurfi, ga karqncin wayewa ga rashin madafa ta yau da kullum, Nima kasada ce tasa na yarda da tayin da akayi min tunda Naga nema ake a tozarta min da iyayen a kunyata su a idon duniya aci mutuncin su". Ita da'i ko motsin kirki ta kasa da gaske gani take duk ya cika dakin, ga wani fitinan kamshinsa duk ya cika Mata hanci. A bazato taji ya Dan shafi gefen fuskarta idan ba kunnenta ne suka jiyo Mata ba da'i dai ba sai taji kamar yace "my previous" a hankali sannan ya Mike Yana fadin "Bari a kawo maganin ki saimu wuce gida tunda doctor yace zamu iya wucewa, Amman yace ki rage yawan tunani Yana haddasa cututtuka". Har dakin Amma Abdul Hakeem ya raka Zahra lokacin duk yawancin bakin sun tafi sai 'yan uwan Amma na Mubi Dana Jimeta sai Kuma Aunty Hasana da take dakon dawowar su, ai tunda magaji ya Kara Kora Mata bayani akan Mahmud ta tafi daga asibitin tunda Mai dungurungum din yazo ita bataga ta Zama ba. Saida ta matsawa Zahrar tayi wanka Tasha tea da magungunan ta kwanta sannan tayi haramar wucewa gida. Sai wurin karfe Tara sannan Hajiya mama ta shigo dakin tana fadin "wallahi daga idar da sallar ta barci ya dakeni sai Dana tashi zilai Mai wanke wanke take fad'a min an dawo da Zahra har sun shigo sun duba ta". "Wallahi kuwa ai jiki da sauki yanzu Tasha magani ta kwanta" "To Allah ya Kara lfy, Wai Hajiya wanene mijin yarinyar Nan ne naji ana fadar Wai cikin Almajiran baba Malam ne, shine nace haba yaushe Alhaji zeyi wannan danyen aikin ya rasa bazai bawa aure Sai a cikin Almajirai". Inna maimuna ce tace "ai mu Hajiya ko waye Alhaji Jafar ya aurawa Fatima wallahi mun karba da hannu biyu mun gode tunda mun San har abada Babu cutarwa a tsakanin Asama'u da dashi da ita Fatiman da abinda ya Haifa bamu taba ganin banbanci ba, Dan haka mun karba da kyakykyawan niyyarsa Allah ta tabbatar Mana da Alkhairi". Gaba daya suka amas "Amin" Hajiya mamar ta Dan jima a dakin kafin ta koma dakinta. Bayan Zahra tayi sallar Asuba ta gama Azkar dinta komawa tayi ta kwanta har lokacin kanta Yana Mata ciwo kadan kadan, sai gurin takwas da rabi Inna maimuna ta tasheta tana fad'a Mata tayi maza ta kimtsa Abbansu Yana nemanta. A gurguje tayi wankan ta fito lokacin an kawo Mata kunun gyada da fanke, kunun gyadar kawai tadan Sha kadan ta shafa lotion dinta ta saka doguwar rigar atamfa ko dankwalin Bata daura ba ta fito cikin takunta na nutsuwa Wanda da yawa mutane ke gani a matsayin yanga da jiji da Kai. A tsakar gidan suka rinka gaisawa da tsirarun yan uwansu na Mubi da sauran ma'aikatan gidan Mata. Da sallama a bakinta ta shiga falon Abban nasu, tayi mamakin ganin kusan duk 'ya'yan Abban suna Nan sai su Ammah da Inna maimuna da kanwar Abban Maman lafia. "Zo nan kusa dani Uwata". Abban ya fad'a Yana murmushi, itama murmushin tayi ta karasa kusa dashi ta zauna nata fadar "Abbana Ina kwana?". "Lafiya kalau Alhamdulillahi Uwata". Sannan ta juya tana gaishe da jama'ar gurin. Said Kuma dakin yayi shiru. Abban ne yacewa Imam "Mai sunan Malam ayi Mana addu'a". Ya jima Yana addu'a sanan aka shafa. Sannan Abban ya Dora da cewa. "Alhamdulillahi ala kulli halin, dole ne mu godewa Allah s.w.a a cikin kowane Hali mutum ya Samu kansa, kowa yasan yanda lamarin Auren Uwata ya ringa kasancewa a baya abune ba Mai dadin maimaitawa ba, to wannan karon ma tarihine yaso maimaita kansa Amma na yanzu sai yafi sauran tada hankali ni Kuma Naga a wannan gab'ar bazan Kara bada wata kafa ba wadda za'a dunga walagigi da rayuwar yarinya karama ba kamar Uwata. Sunanta Ya kira Fatima dago ki kalleni, cikin girmamawa ta dago kanta kamar yanda yayi Mata umarni. Hannunsa yasa ya nuna kansa yace kina ganin zan iya zaluntar k?" Da sauri ta girgiza Kai hawaye na zubo mata. Yace "To Fatima na daura Miki aure da bakon yaron Nan Mahmud na wajen Aminina Malam Bukar". Duk da taji haka daga bakinsa a jiya Amma Bai hanata kara shiga rudu ba saboda wannan taji daga bakin da bazeyi Mata karya ba, Nan da Nan ialahirin jikinta ya shiga rawa wallahi ita a jiyan jinsa kawai take gani take kamar almara ce kawai. Muryar Abbansu ce ta Kara katse Mata tunani "kiyi hakuri Uwata kowa da irin jarabawar da ubangji yake Masa ki dauka taki jarabawar kenan, ki yadda da kaddararki sai Ubangiji ya jibinci lamarinki wannan ba hadin kowa bane hadin Allah ne, kiyiwan mininmi biyayya in Sha Allah zakici ribar rayuwa, ki cire yaron Nan Musbahu daga zuciyarki ki rungumi abinda Allah ya baki. Allah yayi Miki albarka yanda Kika yi min biyayya Allah ya Baki 'ya'ya Wanda zasuyi Miki biyayya kema, Allah ya albarkaci aurenku ya tsone idon makiya da mahassada". Hajiya mama ce ta fasa Kuka tana fadin "Haba Alhaji wannan wane irin danyan hukunci ne? ya zaka dauki 'yar marainyar Allah ka baiwa Wanda ba'asan asalinsa ba, ai duniya saita zage ka Dan Allah ka janye maganar Nan da wannan ba gara kaba salmaun gidan Hajiya Dago ba tunda ya jima Yana son yarinyar Nan Amma ka Hana shi" Kowa a falon kallonta yake ba Wanda ya tofa sai danta Hamza yace "haba mama menene haka kikeyi Dan Allah kiyi shiru da wannan maganar salmanun me Allah ya sauwake me za'a da wannan zuri'ar". Hannu Abban ya dagawa Hamza Yana fadin "ya Isa haka tunda ka Bata amsa basai nace komai ba, Amman ki rubuta ki aje in Sha Allah sai wannan auren ya Zama abin kwatance Kuma abin alfahari duk Wanda ze zageni ya Dade Bai zageni ba, Kuma duk Mai ganin zalunci ne yasa na aurawa Fatima Mahmud na barshi da Allah wallahil Azeem ban taba kallon Uwata a matsayin 'yar wani ba kullum Ina Mata kallon 'yata malak malak a makaranta ne kawai ban saka Mata sunana ba shima nayi haka ne Dan tasan nata mahaifin ta rinka Yi musu addu'a". Addu'a Abban yasa Imama yayi yaba kowa izinin tafiya Amma yace Ammah ta tsaya ita da Hajiya mamar da Inna maimuna da Maman lafia. Aunty Hasana ce ta kamo hannun Zahra zuwa dakin Ammah tana kuka, yarinyar tausayi take Bata kamar yanda Abban ya fad'a ana walagigi da rayuwar ta. Cikin bed room din Ammah suka wuce, bayan sun zauna ne Auntyn ta riko hannun Zahrar "kiyi hakuri kinji Allah Yana sane da halin da kike ciki, Dan Allah kad'a ki watsawa Abba kasa a Ido ki bijirewa auren nan wallahi irin wanna auren Yana albarka fiye da tunanin". Wasu sabbin hawayen ta goge. Cikin shashhshekar kuka tace "wallahi Aunty nifa tsironsa nakeji idan muka hada Ido wani Abu nake gani a idonsa". Sororo Auntyn tayi kafin tace "ban Gane ba tsoronss kamar Yaya, Daman kinsansa ne runtuni?. Kai ta gyada Mata alamar Eh. "Allah ya kyauta" kawai Auntyn tace. "Ko meme ma dai wannan tsakaninku ne kin gyarota can". Ta Mike tana fadin "Bari na koma gida sai zuwa an jima zamu shigo da Sajida da Amatu itama Bata tafi ba jiyan. ********Tun bayan suka dawo daga sallar Asuba Mahmud yake ta faman aiki a cikin laptop dinsa, Yana kallon Sameer Yana kwasar barcin gajiya. Bai gama aikin ba sai kusan karfe takwas na safe, kai tsaye toilet ya nufa ya jima a ciki kafin ya fito daure da towel a kugunsa karami Kuma a hannunsa ya goge sumar kansa me baka sidik Mai laushi Saida ya shirts cikin wani farin yadi filtex marara nauyi ya feda turarensa Alburaq sannan yaje gefen bedside ya dauki wayarsa ya kunna. Abinci ya bukata a kawo musu, yana Gama wayar Kira ya shigo sunan Habib ya gani, ya daga da sallama daga cen Habib Fara fadar. "Habe Dan Allah dukka tadawa Baba malam hankali baka kwana a gida ba abinda baka Saba ba Koda wasa duk dare zaka dawo Amma jiya daga Bari kaje ka dawo shi kenan kayi layar zana Kuma ka Kama ka kulle waya". Dariya yayi Yana cewa "kana tunanin Kona bi dare nayi Gudun auren dole ko?" Shima Habib din dariyar yayi. "Ka Gudun Mana idan ka Isa mai wannan tsaleliyar Ina zaya ya barta koka gudu ka dawo da kafarka, kawai da malam ne ya matsa yaji kana ina". "Ok shi kenan Bari na kira shi Dan hankalinsa ya kwanta Ina Nan tare da Oga Sameer shine ya rikeni nayi Masa wani aiki". Yana kashe wayar ya nufi sofa ya zauna yana janyo stool din da aka Dora abincin. "Oh ni Sameer yaushe na rikeka? ka rikeni dai ka Hanani tafiya ka barni da kame kame ga madam can tana fama da kanta ba mataimaki gaskiya yau in Sha Allah sai kano". Ya fad'a yana nufar toilet shima. Can hayin bankin suka Fara zuwa gurin masu aikin gidan Masha Allah aikin yayi nisa kamar ba jiya aka Fara ba Sam an canzawa gidan fasali kamar bashi ba, duk abinda ake bukata Sameer ya danka shi a hannun Binya. Sannan suka nufi cikin gari. Wani mall suka shiga Mahmud ya jido kayan fruits dasu kayan tea sai chocolates dasu farm fresh yogurt da fresh milk. Leda uku aka cika manya Saida suka dauki hanya Sameer ya kalli Mahmud yana fadin "wadannan kayan fa yallabai na waye". "Dubiya zamu saika Bata tunda ni dai kowa yasan bani da kudin sayansu. 💋❤️ AUREN HUCE HAUSHI 💋❤️ 🔷 Page six🔷 P📖🖋️ ________Sun jima a gurin Baba Malam Yana yiwa Sameer godiyar dawainiyar da yasha akan wannan lamarin, sannan yayiwa Baba Malam din sallama akan zai wuce sai hutu ya Kare zasuzo da mutanen su suna son su kawo wasu ayyukan da za'ayi. Har gurin mota Malam dasu Habib sukayi Masa rakiya, Baba malam Yana fadin "Bari muyi addu'a". Nan yaja doguwar addu'a akan Allah ya tsare hanya, har Sameer ya shiga mota ya fito ya nufi Malam Wanda har ya Fara tafiya, sai Kuma yaja ya tsaya Yana jiran karasowar Sameer din. Dan risinawa yayi Yana fadin "ko za'a samu Wanda ze rakani na Kara dubo jikin wannan yarinyar?" Wani kallon kasan ido Mahmud ya bashi dashi "Wai yarinya". "To! To! Masha Allah ai sai kuje da Mahmud din da Habibu kuga jikin, ai wannan tunani ne Mai kyau.Nima na shiga da safe gurin Alhajin naji yata kwana". Har cikin harabar gidan Sameer ya shiga da motar, Abdul Hakeem Habib ya Kira kafin su shigo ma ya fito Nan Harabar gidan Yana jiransu. Shi yayi musu jagora zuwa falon Abban, yayi murna sosai da ganinsu sun gaisa sosai sun masa godiya sosai da karamcin da yayi musu, yaji dadi sosai Dan har ya ringa tsokanar Sameer Yana fadar "wato tunda kazo gabatar da aikinku ban sake ganin kafarka ba a gidan Nan sai yau dana baku Mata ko? Dan na lura baka da aminin daya wuce Mahmud a garin nan. Masha Allah, Malam ya fada min duk Fadi tashin ku akan lamarin Allah ya saka da Alkhairi yabar zumunci". Suka Amma da "Amin ya Rabbi". Mahmud Alhajin ya kalla Yana fadin "kayi hakuri fa Mahmud munyi maka nauyin kuka". Kai ya gairgiza Yana fadin "ko daya wallahi ba komai nagode, Allah ya saka da Alkhairi ya Kara lafiya Nisan kwana Mai albarka" "Allahumma Amin. Allah yayi Albarka, ya baku zaman lafiya ya baku zuru'a Mai Albarka, sai ayi ta hakuri da lamarin Mata fa. Abdul Hakeem ku shiga ciki su gaisa da Iyayen nasu". Wannan shine shigar Mahmud na biyu gidan, na farko lokacin da magaji yayi accident da mashin suka shigo shida Abdul Hakeem da Hamza ya duba shi a dakin Ammah, dan ma lokacin ba kowa a gidan sunje gaisuwar mutuwa. Directly dakin Hajiya Mama Abdul ya nufa dasu, Zilai Mai musu wanke wanke ce tayi zuruf ta shiga dakin Ammah. Tana fadin "Ammah Ina Jin fa ga mijin Zahara'u Nan sun shiga dakin Mama shida Abdul Hakeem da wasu inaga abokansa ne". Ta juya ta fita. Gyalen Inna maimuna Ammar ta dauka dake kusa da ita ta yafa a jikinta. Da sallama Abdul Hakeem din ya shigo Yana fadin Bismillah ku shigo Mana, a nan kan carpet a kasa suka zauna suna gaishe dasu Ammar tare da tambayar Mai jikin. Abdul Hakeem ne yace " Inna mijin Zahra ne da ubangidansa suka shigo duba ta shi yau ze wuce shine yace a rako shi ya Kara dubata da jikin nata". "Kai Masha Allah an gode madallah Allah ya saka da Alkhairi ya maida ka gida lafiya". Inna maimuna ta fada sannan ta kara da cewa "to waye angon nawa Dan nice ta karfe ita wannan Farafarar ba wani abun azo a gani zata iya ba ni kuwa ko banza na tuka maka tuwon dawa da man shanu ko ba haka ba?" Ta tambaye shi tana kallonsu. Duk dariya sukayi Amma shi gogan Dan murmushi yayi kadan Yana basarwa. Abdul Hakeem ne ya nuna Mahmud Yana cewa. "Ga angon naki nan nagama kamar kunyarki yakeji" "A'a! Masha Allah tubarakallah Mai gidan nawa wanke hannu daka taba ne, kaga dago ka kalleni ni Kaka ce kada kaji wata kunya ta". Kara sadda Kai yayi shifa duk jinsa yake wani iri Wai shine a zaune a dakin surukai Ashe da gaske ana jin kunyar shi wallahi da ji yake kawai fada ake ba wani nauyin da akeji Saida ya same shi yanzu yake gaskata hakan. A kaikaice Ammah ta kalleshi "Masha Allah" ta fada a zuciyar ta, ita bataga wata makusa ba a tare dashi Kuma idan ba idon tane yake Mata gizo ba sai taga duk cikin Wanda zasu auri Zahrar a baya bataga Mai nagarat wannan yaron ba. Albarka da nasiha dai ya Sha ta gurin Inna maimuna. A haka suka fito daga dakin har suka fito compound din Abdul Hakeem Bai fito ba sai duba agogo Sameer keyi Yana mita. "Nifa bana son nayi Rana a tafiyar Nan gaskiya, Naga alamar kuma neman kuke kusa nayi yamma ma". Kafin Mahmud ya bashi amsa Abdul Hakeem din ya fito da sauri da key a hannunsa Yana fadin "kuyi hakuri key din ne ba'a gani ba da wuri ku karaso ciki kafin Zahrar ta fito ku gaisa". Mahmud ne yace "Kai haba da an kyaketa ta huta ita da Bata da lafiyar kirki". Karamin falo ne da kujeru masu kyau sosai da kayan kallon alama an tana deshi ne saboda Yara Mata na gidan da Kuma dai dai kun Baki. Bayan fitar Abdul Hakeem, Sameer ya kalli Mahmud. "Dan Allah my man yaushe idonka ya koyi kunya? Naga sai wani sadda Kai kake, nifa lamarinka ya Fara bani tsoro na rasa wace alkibla ka kalla kazo garin mutane ka Mike kafa kana wata irin rayuwa a takure nace zan dauki mataki ka aje min sharadi, da kasan bazan it's tsallakewa ba, yanzu Kuma Rana tsaka a tarko aure Kai kadai kamar marar gata sai walagigi kake alhalin kana da madafa". Tsaki yayi " kana da matsala wallahi ko me zance fada maka bazaka Gane ba, amma idan lokaci yayi zaka fashinmta,yanzu duk bayanin da zanyi maka ba fashinmta zakayi ba, kawai mu bar maganar kawaai" Kanshin turaren ne ya alamta musu zuwanta. sallama tayi cikin siririyar muryarta. Sameer ne ya amsa Mata sallamar a zahiri Dan shi Dan gogan a saman lebensa ta amsa sallamar. Sameer din ne ya Dan Mike Yana fadar. "Masha Allah jiki yayi sauki kam, "Bismillah". Yana nuna Mata kujerar gefen Mahmud. Kai ta dangirgiza Masa tana dan murmushi kasa kasa. A Nan kan carpet ta zauna daga gefe tana gaishe da su a jimlace. "Lafiya kalau" Sameer ya amsa Yana fadin "ya jikin naki?" "Alhamdulillahi" ta amsa masa. Sai Kuma duk sukayi shiru, ganin lokaci Yana qurewa Sameer ya Mike tare da kallon Zahra Yana fadin " To madam bako zeyi halinsa Allah ya bada zaman lafiya. Amma fa sai kina hakuri da halinsa gaskiya ba kirki ya cika ba Ina son idan na dawo Naga canji na zahiri a tare dashi, sunan Sameer Sa'ad koko, zeyi miki cikakken bayanin koni waye a gurinsa Allah ya bada zaman lafiya da zuri'a mai..albarka Allah yasa next year by now muna bkin suna" Da sauri Mahmud ya kalli Sameer a zuciyarsa Yana fadin "Allah ya shiryeka Sam baka girma". A hankali tace " Mun gode kwarai Allah ya tsare ya kiyaye hanya". "Amin" ya amsa Yana kallon Mahmud. "Ni zan wuce saina sake shigowa ayi kokarin ganin aikin Nan ya kammalu". Ya fada Yana nufar kofar fita. Sai lokacin Mahmud din yayi magana "pls ka jirani minti biyar Dan Allah". "Idan ya wuce haka Kam...." Ya fice ba tare daya karasa fada ba. Tunda Sameer din ya fita take wasa da karamin zoben da yake hannunta. Bata dagon kalle shi ba shi Kuma Bai tofa tasa ba amman idonsa Yana kanta, Kare Mata kallo yake Yana fadar "Masha Allah tabarakakkahu ahasanil kaliqin". Tsam ya taso daga inda yake ya sauko kasa inda take zaune. "Ya jikin naki?". Ta tsinkayi maganarsa kusa da ita daf Sam bataga lokacin daya taso ba. Cikin daburcewa saboda kusancin nasu yayi matukar yawa ji tayi kamar ma iskar gurin ta tsaya sai munfashinsa take shaqa kawai. A mamakance taga yasa hannunsa ya dago fuskarta suka hada Ido hudu dashi. Da sauri ta runtse idanunta zuciyarta na wata irin bugawa. "Bude idon Kona Baki mamaki". Marmar ta Fara da idon tana budewa a hankali Amma taki kallon nasa idon. "Ya jikin?". Ya Kara maiamaitawa, a hankali ta bude bakinta tace "da sauki" Gamshin Lister mint ne ya daki fuskarsa. Banda Yana daf da ita ba yanda za'ayi yaji abinda ta fada. "Allah ya Kara lafiya". "Ameen" Ta fada. Hannunsa ya cire daga fuskarta yana Dan furzar da iska daga bikinsa ya Mike tsaye, a hankali ta sauke wani numfashi. A bazata taji yace "bani wayarki" Ba musu ta Mika masa, aljihu taga ya saka Yana fadin "ki shiga gida ki kwanta kiyi barci sosai kada ki yawaita hayaniya ki samu hutu sosai, zan tambayi magaji idan bakya hutawa yanda ya kamata ni Ina da inda zan kaiki ki samu isolation, tashi muje ki shiga gida ana jirana". Saida ta shige ciki kafin ya juya ya nufi gurin da Sameer da Abdul Hakeem suke suna Hira. Lokacin data shiga dakin ta Samu Aunty Hasana dasu sajida sunzo har da yaran duka. Da guda ta karasa cikin suka rungume juna da Sajida Nan da Nan sai hawaye itama sajidar kukan ta fara. Ammah ce tace "Naga abinda ya isheni meye haka zaku tasa mutane a gaba Kuna kuka, to kukan maganin me ze muku aikin Gama ai ya Riga ya Gama Saida hakuri da addu'a kawai". Uwar dakin Ammah suka shige. Magaji ne yayi sallama ya shigo da manyan ledoji guda biyu niqi-niqi da kaya Auntyn Hasan na tambayar"daga Ina?" Ya fice da sauran Yana fadin "ina zuwa Aunty" Wata ledar ya shigo da ita Yana fadar"kayan dubiya ne aka kawo Mata" ledar daya kawo daga karshen ya bude rafar 'yan dari bibiyu hura biyu ya dauko daga saman kayan, Aunty Hasana ya Mikawa yana fadar "gashi nan inji abokin mijinta Wanda suka shigo dashi dazu". Godiya su Inna maimuna sukayi tayi kamar Yana nan a gurin suna ta Saka albarka. ********* Bayan tafiyar Sameer can gurin aikin gidan suka wuce, ba karamin mamaki Habib yayi ba har ya kasa hakuri ya tambayi Bilyaminu lokacin Mahmud Yana ciki. "Dan Allah wane irin kudi gayen Nan ya bada haka Nan da Nan gidan ya juye ya Zama kamar daukowa akayi daga wata kasar". "Wallahi Nima bazance ga abinda ake kashewa ba, iya kudin aiki Dana abinci kawai suke a hannuna, bakaga wash bakin fuska ba su biyu?' "Eh nagansu" Habib ya fada. "To ai tun jiya sukazo da komai na aikin bakaga Nata'ala ba shima lebura ya koma kaga ai da malam shi yasa a Kira saboda 'yan gyare gyaren amman da masu iyawar sukazo shima yaronsu ya koma". Ya fada Yana dariya. "Wallahi Bilya sai a kyaleka Kai kowama sai ka tab'a". "Gaskiyar kenan ni wallahi burgeni ma yayi tunda baiyi zuciya ba ya tafi, ko banza nasan Yana lure da koma Dan gyaran nasa aikin". *****A bedroom din ammah Zahra ce da Sajida suke tattaunawa akan abinda ya faru,sunyi iya nasu hasashen amma sun kasa gano bakin zare Sajida ce tace "nifa Zahra Ina hasashen wani Abu akan lamarin ki" "Kamar me kenan?" Dan Jim tayi kafin tace "Anya ba asiri ake yiwa duk wani Wanda yazo da niyyar aurenki ba? Ki tsaya kiyi nazarin abun Mana ko mafarkan da kike yi duk lokacin da maganar aurenki ta taso abin dubawa ne" Dan murmushi Zahrar tayi "kin jiki kema bestie wane irin asiri Kuma,ana zaune lafiya to waye har ze bata lokacinsa da kudinsa gurin yi min wani Abu kawai daga Allah ne kinsan kowa da yanda Allah make jarabtarsa ni tawace tazo a haka". "Eh na yarda daga Allah ne bana inkari Amma akwai sanadi, inaga gobe ma zan wuce duk da nacewa Umma sai Wednesday Amma na fasa wallahi Rimi zanje gurin Baban Umma na fada Masa ai kinsan shi farin sani Kuma zeyi duk abinda ya kamata tunda ke wani lokacin kanki ba Maths". Kwarkwar tayi da ido Dan Allah Saji kada ki tafi ki Bari a Gama komai saiki tafin". Wani kallo tayiwa Zahra "tafiya dole na tafi Amma zan dawo kwana kusa in Sha Allah, kinsan Zama da Baffa yasa Ina Gane wasu abubuwan tunda Yana fadw min ire -iren abubuwan da suka shafi sihiri Kinga yace min duk wani ciwon da yake da lokaci misali ace kullun sai dare mutun yake kasa barci kinsan da matsala, ko ace mace duk ranar girkinta Bata da lafiya ko duk ranar girkinta tana zubar da jini amma idan ta Gama aikin shike nan sai ya dauke babu, ko kamar taki matsalar sai an saka Miki ranar aure sai ana gaf da biki abun yake lalacewa, Kika sani ko Abban naku ma ya Fara irin wannan tunanin ne yasa ya yanke wanna hukuncin cikin sirri ki tsaya kiyi tunani Mana" Sosai magungunan Sajida sun sakata a tunanin da Bata tabayi ba. Sauke zazzafan numfashi tayi tana fadin "Allah ya kyauta ni duk kin sakani a tunani wallahi" Haba "Bestie ai kinsan ruwa baya tsami a banza me ake nema a gurin mace Allah Bai Baki ba Amma sai an Yi abu kama-kama ya lalace zance da muka Dade munayj da Aunty Hasana kenan jiya Kuma ta bain go ahead na naje na faduwa Baffan rimin, tace ma zata fadawa Ammah, ma". Kiran da Aunty Hasana tayi wa Sajida ne ya katse musu tattaunawar, ta tashi ta fita. Washe gari duk bakin Ammah suka tafi, Inna maimuna kadai suka Bari sai Amarya taje dakinta zata koma gida. Part din da bakin suka zauna Ammah tasa su Zilai suka gyara sosai tunda Daman nasu Zahra ne, kafin yamma gurin yayi tas kamar ba'ayi wata dabdala a cikinsa ba. Bayan sallar insha'i zahra da Sajida suka koma part din. Suna zaune a kan gado Autan Ammah musaddiq ya shigo dakin da sallama hannunsa rike da leda fara Mai kyau ya mikowa Zahra yana fadin "gashi Aunty inji wannan na gidan Baba Malam din yace a kawo Miki Kuma yana duba ki, Kinga Nima ya bani". Ya Mika nata 1 k din dake hannunsa.". "To angode madallah". Ledar Sajida ta dauka ta bude waya ta gani sabuwa kar a ciki. "Wow gaskiya ba karya ke! Irin wannan babbar harka haka, Dan Allah Yi min bayani naji yace wannan na gidan Baba malam din waye ko angon namu ne da ake Raina mana ya Fara tsula Mana abun arziki haka?". Baki ta Zahra ta zunbura. "Nace Masa Ina bukatar sabuwar waya ne da zai kawo min, ni wallahi a mayar Masa". Ta fada tana kokarin amsar ledar faga hannun sajidar. "Ke tsaya da Allah yi min bayani yanda zan gane, Ina taking wayar naji kina wata magana". "Tana gurinsa tun safe ya karba ni bansan abinda zeyi da ita ba, ya dai ce na bashi kawai ni kuma na bashin shine Kuma maimakon ya bani tawa shine ya Aiko min da wannan". Musaddiq Sajida ta kalla 'kai auta maza kaje kace tace ta gode Allah ya Kara nudi" Sai da ya fita sannna ta juyo gurin Zahra. "Amman wallahi kin bani mamaki Allah ya tarfawa garinki nono ki nemi ki Bata rawarki da tsalle to kici gaba har ki nuna b'araka a gaban 'yan uba, Koda wasa kara ki Kara ba'a yiwa miji haka ko bakaso Abu baka nunawa a gabansa, kika san da Yaya yayi sawo Miki danya faranta Miki Rai Amma Zaki wani kwasale shi kice a mayar Masa kina son tun yanzu ki kashe Masa Gwiwa ko". 💋❤️ AUREN HUCE HAUSHI💋❤️ JINJINA TA MUSAMMAN GA MALAMAN MAKARANTA ALLAH YAYI JAGORA YA QARA BASIRA DA JURIYAR SAUKEN NAUYIN DA AKA DORA MUKU NA AMANAR YARA QANANA👫👫👫👫👍👍👍✍️ ✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨ This page is deducted to you Families of late Alhaji Isah Musa Bakin kasuwa kazaure jigawa state. 🔷PAGE SEVEN🔷 _______Mika tayi tana salatin ma'aiki s a.w.w sannan ta Zoro kafafunta kasa, tunda ta farka tasan tabbas karfe biyu tayi na sulsulin dare har ya zamar Mata jiki. Dubanta ta kai inda Sajida ke kwance barcinta take sadidan cikin kwanciya hankali, sai taji Ina ma ita ce haka, wasu hawayen ne suka ciko idanunta a hankali tace "Ya Rabbi ga baiwarka Mai rauna ka jibinci lamarina dan Isar Manzon Allah s a.w.w. kada ka barni da iyawata ka iya min da iyawarka kada ka Bari makiya su yi min dariya ka bani rinjaye ka dorani akan duk Wanda yake son Hawa kaina". Ta Mike tsam ta nufi toilet din cikin dakin sai Kuma ta fito saboda shaf ta manta kafin su kwanta taga famfon ya dauke Kuma da alama ba'a kunna layinsu na tanki ba. Cikin rashin tsoro ta bude kofar ta fita zuwa bayan part din Mama don ta kunno ruwan, gurin ta dosa gadan gadan sai Kuma tayi turus, magana take jiyowa daga wurin da sauri ta koma baya dan bata San abinda zata gani ba. Tana tsuma ita fa duk da Bata da tsoro amma tana tsoron ganin abinda yafi karfin idonta ko Kuma wani mugun abun. Dole tayi hakurin yin sallar a koma ta kwanta tana ta sake-sake har kusan Asuba, ba Kuma taji motsin wani na tada hankali ba. Saida Sajida ta tashe ta lokacin har an Fara sallah a masallacin gidan nasu. A gurguje tayo alwala da alama Sajida ce ta shigo da ruwan. Bayan sunyi sallah zaman Azkar sukayi har lokacin da gari yayi shahhh alamar wayewa, sannan suka koma suka kwanta. Dukkan su ba barci suke ba, Zahra ce ta danyi tsaki kadan ta tashi zaune. Kallonta Sajida tayi. "Yaya Bestie akwai damuwa ne?" Dan juyowa zahrar tayi tana kallon sajidar tana Kara wani tsakin "nifa wallahi na fada Miki tsoron mutumin nan nakeji tun ranar Dana Fara ganinsa a gidan Baba malam nake Jin wata irin shakkarsa. Dan Allah a haka zamu rayu bana ko son kallon idanunsa? Kinsan wani tarin abin haushin jiya fa hannu yasa ya dago fuskata Wai dole saina bude idona na kalle shi ko Kuma ya bani mamaki, Kuma fa ranar Nan a asibiti har wani shafar min fuska yayi Yana fadar nayi hakuri da wannan hadin shima ba so yake ba, kawai yayi biyaya ne tunda baze iya yiwa su Abba musu ba, amma ni Ina iya fada musu bana so". Baki Sajida ta rufe tana kunshe dariyar ta. Kai ta shiga girgizawa tana fadar Babbar magana ki fadawa su Abba bakyaso! Wato ke ga marar ta ido ko? Shima har yasan kimarsu da baze iya yin musu dasu ba saike ce marar kunya Zaki Fadi Baki so, ki rabu dashi kwaai abinda nake so dake yanzu ki koyi dakewa a gaban nasa sannan ki daina tsoron idanun nasa, Wai tsaya fada min menene a cikin idon nasa da yake firgitaki duk girmanki da wayonki da wayewar ki?" Wani shagwabe fuska tayi kamar Mai Shirin fasa kuka. "Bazaki gabe ba, ni kaina bansan ya zanyi ba saboda shi fa na daina zuwa gidan Baba malam tunda lokacin kullum Yana tare da shi kuma sai yayi ta kallona yana tsareni da wadannan idunuwan nasa kamar Mai jin barci". Yanzu dariya sosai Sajida keyi harda kwalla tana fadar Babbar magana tab kice abin asali ya Samo shi ai kaya ne suka tsinke Masa a gidin kaba kece dai kike bulayi" "Kamar yaya?" "A'a bazakiji mutuwar sarki a bakina ba ai tunda an hada anyi Mai walahar...". Sautin kiran waya ya dakatar da shegantakar da sajidar ke mata. Wayar da aka kawo Mata jiya ce ta dauki kida, Sajida ce ta Mika hannu ta dauka M.M DANGE ta gani Yana yawo akan screen din. Zahra ta mikawa tana fadar oga ne da alama a Sha soyayya lfy. Tayi waje tana fadin Bari naje nayiwa Ammah shara. Bata daga Kiran ba har Saida ya kusa katsewa kana ta daga tasa a kunnenta. Daga can taji Yana fadar "Assalamu Alaikum warahamatullahi ta'ala wabarakatuhu". A zuciyar ta a amsa Dan da gaske in dai zata ganshi ko taji maganarsa kasa samun nutsuwa take. Sake maimaita sallamar yayi, da kyar ta amsa masa tare da fadar " Ina kwana?" Shiru taji ba'a amsa ba kamar ma an sauka daga layin, amma ga mamakinta tana dubawa sai taga Yana nan, itama shirun tayi kudin sunata tafiya saita saka handsfree ta aje wayar kusa da daga gefe tana kallon ikon Allah. Saida ya mula Dan kansa "yace ya jikin naki I hope kin shan maganinki?" "Eh" ta fada a takaice. "Fine"yace shima a takaicen. Ita mamaki ma yake Bata har wani turanci yake jefawa a magana kamar gaske. "Sai an jima ta fada tana kokarin katse Kiran. "Kada ki kuskurs ki kashe min Kira" ya fada in serious tongue. Shiru tayi tana mamakinsa sai wata izza yake Mata kamar wani abin azo a gani. Muryarshi ta tsinkaya Yana fadin ki bude data na turo Miki sako idan da abinda kike bukatar ayi ko a Kara sai ki fada min, take care". Kit ya kashe kiran. "Kutt!" Ta fada "amman gayen nan yama Raina ni wlh Wai kada na kashe Masa waya" Kwafa tayi "zakaga na kiraka ganin idon ka" ta Jafar da wayar tana mita. Taso yin barci Amma ta kasa dole ta hakura, wayar ta Kara daukowa tana kare Mata kallo. Number din Hameeda ta Fara sakawa tunda taga sabon layi ne ya dauke natan, ga mamakinta sai taga sunan Hameedar ya bayyana ba bata lokaci ta kira. Tana ta ringing kamar baza'a dauka ba sai Kuma ta daga da sallama ai tana jin muryar Zahra ta Fara mita "yanzu Dan Allah kin kyauta tun jiya nake neman layinki Amma shiru na Kira Mama nace ta Baki tace min bakya Jin Dadi kina barci, wallahi Kinga yanda hankalina ya tashi kuwa ki Bari lokacin da Sajida ta fada min halin da ake ciki wallahi daba final muke ba Allah da barinta zanyi c/o na taho gida har fada mukayi da Salma Wai ai sai inje na baiwa Mushahun hakuri ya dawo ya aure maganganu dai gasu nan ki Bari kawai ai jibi zamu Gama in Sha Allah komai dare a gida zan kwana". "Allah ya yarda ki Bari kawai wallahi Ina cikin yanayi akwai damuwa Dan Allah kizo ko naji sauki abubuwan". Ta fada tana share hawaye, sukayi sallma Dan it ma Hameedar kukan take. Wai ita Mushahu ya yiwa haka, duk wadanda suka fasa aurenta Bata taba Jin Wanda ya Bata Mata Rai ya Kuma tsaya Mata kamar wannan ba ai ko wace irin matsala ce ita ya kamata ya Fara fadawa ba ya yanke mu'amala da ita ba a lokacin da take matukar bukatarsa ya manta shakuwar dake tsakanin su da alkawarirrikan da suka yiwa juna. Kwantawa tayi tana tunanin baya a haka wani wahalallan barci yayi gaba da ita. **********Tun Yana tsammanin ganin ta bude data ta duba sakon har ya cire Rai da hakan. Lambar Abdul Hakeem ya Kira sun jima suna waya kafin suyi sallama. Laptop dinsa ya janyo yaci gaba da aiyukansa sai kusan azzahar ya Gama. toilet din cikin dakin ya shiga ya dauro alwala,a masallacin hotel din Yaya sallah lokacin daya fito Kiran Habib ya shigo Masa "Wai Dan Allah kana Ina ne tun dazu muke nemanka kazo masu aikin hada furniture's din Nan ne suka Gama da cabinet din kitchen". "Ok gani Nan inaga kada kayi nisa zuwa an jima su Aunty zasuzo suga gurin" Ya fada. Yana nufar gurin da ya saba aje lifan din Habib. Wayar Ammah Abdul Hakeem ya Kira ya fada Mata Mahmud yace a turo a gano gidan an Gama gyaran, dakin Mama Ammah ta shiga ta fada Mata sannan Kira Aunty Hasana ta fada Mata kafin ta wuce gurin Alhajin ta fada Masa tunda shiya dawo daga gidan gonar sai su Abdul Hakeem ya baro suna yiwa shanu Allura da Basu magunguna. Wurin karfe biyar Aunty Hasana ta debesu a mota harda Sajida suka nufi Hayin bankin cikin jagorancin Habib, lokacin Inna Bata Nan taje MIYA gurin wata aminiyar ta da sukayi aikin Haji shekara daya. Duk cikinsu ba wadda Bata kadu da ganin gidan ba domin ba karaya an narka mahaukatan kudi a gidan bazaka tab'a cewa renovation akayi Masa ba, bedroom's ne guda uku biyu suna kallon juna dayan Kuma daga gefe da alama yafi sauran girma Kuma shi kadai ne a rufe, sun zagaya ko Ina sai santin gidan Sajida tace tana ta daukar video, falon kadai abin kallo ne duk da ba komai a cikinsa sai fitilu da aka kunna sai Kuma AC da aka ware. Hajiya mama ce ta kasa hakuri ta leka ta Kira Habib Nan falon ya shigo Yana fadin "gani Mama" Yana Dan rankwafawa. Aunty Hasana mama ta kalla "Hasana Dan Allah ki tayani tambayar yaron Nan tunda shi namu ne na gida baze cucemu ba, Wai wannan yaron sana'ar me yake daya iya Kama hayar wannan uban gidan"?" Kara risinawa yayi Yana fadar "ba haya ya Kama ba Baba malam ne ya bashi kyauta, sai Kuma kungiyar yake yiwa aiki suka kawo masu aiki suka yiwa gidan 'yan gyare -gyare harda kayan daki ma suka zuba masa, Bismillah Bari na bude muku ku gani yanzu ba dadewa zuka Gama hadawa da kitchen din suka tafi". Dakin ya bude musu ba Hajiya mama da take ta kwana biyu ba, ko Aunty Hasana da Sajida Saida suka Zama 'yan kauye Dan tunda suke Basu taba ganin irin wanna gadon a zahiri ba, ita kanta aunty Hasana lamarin Yana neman ya gagari tunaninta fa ance Almajirin Baba malam to Amma idan aka saka mizanin hankali abin yafi karfin yanda aka fada to wane irin NGO's ne da suke irin wannan aikin akan daidaikun ma'aikatan su haka?" Gaskiya abin akwai abin dubawa. Lokacin da suka fito harabar gidan ne wata Hilux ta shigo da kaya a bayan motar mutane uku ne a motar bakar fata biyu fari daya Kamar balarabe Kamar kwara. Kameme Hajiya mama ta hanasu tafiya sai da aka sauke kayan ta gani abinda da suka Gane irin katuwar plasima din Nan Mai cin Rabin bangon Nan ne kawai amman sauran tarkacen Basu Gane komai ba, haka suka kada suka tafi mama nata mitar "A'a da sake Alhaji ya titsiya yaron Nan saiya nuna Iyayen shi kafin a Kai Masa yarinyar Nan haka kawai aje ayi kitso da kwarkawata mutanen yanzu ba abin yarda bane sai kaga mutum har mutum Amman a Baki malam a ciki Kuma Fir'auna". Maganar data Basu Aunty dariya kenan. 💋❤️ 💋❤️ 💋❤️ AUREN HUCE HAUSHI 💋❤️ 💋❤️ 💋❤️ STORY AND . WRITTEN BY MAMAN FATIMAH PAGE EIGHT Lokacin da suka shigo gidan ana ta kokarin daura alwalar sallar magariba. Sai bayan sallar insha'i ne Mama ta shigo dakin Ammah suka hadu da Aunty Hasana suna fadawa Ammah yanda suka gano gidan da Kuma yanda abin ya daure musu kai. Nisawa Ammar tayi tana fadar "Mama ki Sami Abban kiyi Masa bayani yanda ze fahimta kinsan yanda suke da malam bana tunanin wannan abun ze saka ya canza ra'ayinsa duba da yanda ya yanke hukuncinsa Bai nemi shawarar kowa ba". "Aiko dai ya kamata ayi wani Abu gaskiya Nima lamarin ya tsaya mini a cikin zuciya". Aunty Hasana ta fada. Sun jima suna tattaunawar kafin Mama ta koma daki tabar Autty Hasanar da Ammah. Zama Aunty Hasanar ta kyara ta fuskanci Ammar ta Kira sunanta "Anya wannan Mahmud din ba abinda yake boyewa kuwa Ammah Kinga gidan kuwa ga wannan uwar wayar daya canza Mata kinsan kudinta kuwa ? gaskiya I doubt much, ni dai kiyiwa Abban magana da kanki Kamar zefi daukar abun serious akan na Mama". Can Kuma sajida ce tasa Zahra a gaba tana ta faman zuba. "Innalillahi! Kinga gidanki kuwa? Allah ya bamu ya taku wallahi Zahra ki godewa Allah. Wallahi Allah ya Gama miki duk wata ni'ima ta ko Ina kinyi gaban da Nan kurkusa dai kafin a fiki za'a Dade ana lalube. Zahra Naga mijinki har mun gaisa ada Ina adawa da auren Amma tunda na ganshi Naga Yana yinsa nasan yanzu ne kikayi aure da mijin daya Dace ke.Kawai dai matsalar za'ace ba Mai kudi bane,amma a yanda gidan da zaya ajeki yake wallahi ko minister ne sai hakan, akwai abinda na gani a gidanki wallahi ban taba gani a gidanki kowa ba duk yawona sai dai a film amma dai a zahiri A'a ban taba gani ba Allah Bai kaini gurin ba". Tunda ta Fara zuba Zahrar ke bin sajida da idon lokaci daya duk ta wani rude sai zuba take Kamar 'ya 'yan kanya. "Kin Gama?" zahrar ta tambayi sajidar. "Eh na Gama aini an ma yanka ta tashi na fasa tafiyar zanyi waya da Mom taje can Rimin sumailar gurin Baffan kawai, tunda Daman zatazo nan din ba suna kwantagora". "Ke Kika sani dai tunda Naga kina nema ki Zama wata daban ko dai an canza min ke da wata ne ko Kuma wani abun ya fada Miki ya goge Miki hadda ne?". "Eh da alama Kam Dan ya fiki iya lafazi gaskiya inaga na Zama 'yar team dinsa fa tunda Naga ke Baki da wayo". Ta fada tana dariya. Washe gari tun safe Abba yasa aka Kai furniture's din Zahra gidan Daman Aunty Hasana sunyi magana da Wanda zasu hada musu kayan, kayan kitchen da sauran kayayyakin duk suna gidan Aunty Hasana daga can aka ringa daukowa, masu aikin su suka hada komai na gidan hatta kitchen su suka gyara komai, gidan ba karamin kyau yayi ba, ba karya duk Wanda yaga gidan yasan na 'yar gata ne.Dan wasu irin mahaukatan Turkish furniture's ne wanda kakanninta ta gurin uwa sukayi Mata duk wani abun more rayuwa akwai shi a gidan Nan, bangaren electronics ma sai a cikin lockers aka zuba wasu, komai yayi. Lokacin da aka Gama gyaran Aunty Hasana da sajida ne sukazo gani ba karamin burgesu gidan yayi ba Dan sai yanzu ne ya fito a asalinsa na kyau da kayatar da Mai gani, komai na gidan unique ne Masha Allah. A waya sajida ta daukowa Ammah komai. Ita kanta Ammah Kai Kawai take jinjinawa Dan ba karamin burgeta abin yayi ba, sai dai can kasan ranta rudani ne kala-kala domin abin ne duk yazo a hagunce. Tana tsoron lamarin sosai sai da har abada baza iya jayayya da Alhajin ba Dan da gaske ubane tsayayye Wanda baya nuna banbanci tsakanin abinda ya Haifa da Wanda yake bashi ya Haifa ba, amma harga Allah tana zulumin wannan AUREN HUCE HAUSHIN da Alhajin yayiwa 'yar marainiyar Allah, mazan yanzu sunce suna sonka ma ya kukan kare idan Zama yayi Zama ballantana matar cushe ta San komai Daren dadewa ranar da yaga irin matar da yake so Sai dai zahra tayi hakurin zama Kawai, duk da tasan Bata da haufi akan yarinyar Tata Dan macece har mace abin alfaharin kowa ne namiji ace ya mallaki Kamar ta, to Amma shi lamarin so daban yake duk kyan mutum da asalinsa ba lallai ne ace yana burge kowa ba domin shi dai so makaho ne. Ajiyar zuciya ta sauke a hankali duk jikinta yayi Mata wani irin Sanya ta kalli Aunty Hasana tace "Hasana Ina jin wani irin rauni a zuciya ta game da lamarin nan Ina tausayin yarinyar nan rayuwa tana ta walagigi da ita sai nake ganin Kamar laifi nane Dana kafe a barmin yarinyar Nan na hana kakanninta ita ni Kuma nayi sakacin da aka maida rayuwar ta Kamar kwallo ana ta dokata daga Nan zuwa nan". Ta karasa maganar hawaye na zubo mata. Abinda tunda Allah ya kawo Aunty Hasana duniya Bata taba gani ba a zahiri gurin Ammah Nan da Nan hankalinta ya tashi sajida ma kukan ta Fara duk da batasas takamaimai man abinda ya saka Ammah kukan ba, tashi tayi ta fice daga dakin jin an Fara Kiran sallar magariba. Aunty Hasana ce tace "Haba Ammah duk yanda Kika jure bakin cikin baya na abubuwan da suka faru Baki taba zubar da hawaye ba sai yanzu da Allah ya nufa akayi ai godiya Zaki yiwa Allah daya kawo karshen wahalar ba kuka ba". Gefen zani tasa tana goge hawayen. "Hasana Ina hango abinda ke bakya hangowa ne,masu iya magana suna cewa matar shige Bata daraja ba irin wannan rayuwar na sowa Zahra ba to sai dai kana naka Allah Yana nasa Kuma nasan ne gaskiya. Ba komai haka Allah ya tsara komai mukaddari ne daga gare shi, naji Alhaji Yana maganar zuwa juma'a za'a kaita". *******Tun bayan kammala karatunsu na bayan insha'i da suke na littafin iziyya yake zaune a kusa da Baba malam har kowa ya watse ya rage saura su biyu tunda malam yaga haka yasan da magana a bakin Mahmud ne. "Ya ya akayi ne Mahmuda?" Malam ya jefo Masa tambayar, Kara dukar da Kai yayi kafin yace "Daman maganar kayan lefe ne dazu Oga Sameer ya kirani yace ya hado tasa gudunmawar kenan, shine nace Bari na fada maka Dan kasan da zuwansu". "Ikon Allah shi wannan yaron baya gajiya ne Kamar baisan ciwon nema ba tunda yazo ya riski maganar Nan yake Yi kan jiki kan karfi. Allah ya saka Masa da Alkhairi yabar muku zumunci". "Ameen" ya amsa. Harya Mike ze tafi sai malam din ya dakatar dashi, dawowa yayi zauna. Gyaran murya malam din yafa kafin ta jefo Masa tambayar. "Sai zuwa yaushe ne kake ganin zamuje ga mahaifan naka kaga dole muje musu tunda wannan lamarin ya faru". Kai ya sadda kasa Yana fadin "zamuje in Sha Allah Amma Dan Allah a Kara min lokaci da kaina zanyi maganar ayi hakuri". "To ba laifi Allah ya iya Mana kaje ka Samu su Habibu kuje acan gidan ku kwana kaga sun zuba dukiyar kasan yanzu mutum ake kiwo ba dabba ba". "To in Sha Allah za'ayi hakan amma ni Ina Nan sai dai su Habib din suje". "To ai hakan ma yayi Allah yayi Albarka". Saida ya dudduba dakunan yaran ya tabbatar da komai lafiya lokacin sha biyu ta wuce, dakinsu ya nufa wanka yayi ya saka kayan barci sannan ya hau gado ya bude laptop dinsa. Email dinsa ya shiga Yana duba sakknnin daya samu sakon daya shigo ne ya dauki hankalinsa. "Ya Salam!". Abinda ya iya ambata kenan sai Kuma sautin daddad'an ringtone dinsa ya karade dakin. "Sameer!" Ya fada a hankali yasan za'ayi haka, ya haga wayar Yana fadin "Ta Yaya hakan ya faru?" Daga can bangaren Sameer din yadan furzar huci Mai zafi Yana fadar "wallahi nayi duk yanda zanyi Amma abun yaki yuwuwa dole ka daura ka kawar da komai muje gaskiya Dan kasan tunda akaje Nan zuwan nake ne Kawai mafita". "Amman ai kasan halin da ake ciki so kake ace na gudu nabar 'yar mutane Eyeh?". "Cool down Mana my man abin Bai Kai nan ba aikin daine ya taso na gaggawa Kuma dole sai da Kai za'ayi Dan haka suyi hakuri su aje maka ita zuwa sanda ka dawo ko Kuma ka dauko abarka ku tafi, kaga ai tafiyar tafi yi maka armashi ko?" Ya fada cikin zolaya. "Dan Allah ka Zama serious mana, kayi duk abinda ya kamata a Nan goben ka hakura da zuwan ka turo wannan friend din naka tunda yasan gurin ya kawo kayan kawai, Kai Kuma ka Kira Baba malam ka fada Masa daga can sun nemi ganin wakilansu na kasa da jahoshi da kananan hukumomi nasan dai kome ake ciki baze wuce kwana buying zuwa uku ba kaga lokacin na tare a gidana nafi son na barta a Nan gidana akan na tafi Bata tare ba". "Ko dai.......?" Sameer ya fada Yana dariya. "Allah ya shiryeka ko dai me? kasan ni salihn ne ba ruwana da wannan sabgar sai ku". Kit ya kashe wayar sannan yayi switch off dinta. Misalin karfe Sha biyun Rana wata tamfatsetsiyar mota Parker a kofar gidan malam. Akwatuna Yara suka dunga saukewa suna shiga falon malam saida suka Gama sannan baki nufi falon malam din bisa jagorancin Habib sun gaisa sosai da malam suka gabatar Masa da kayan daga Sameer. Malam yayi godiya ya saka Albarka ba adadi. Falon malam ya bar musu sukaci abinci suka huta sannan Habib ya rakasu can gidan suka gaisa da Mahmud din. Sai bayan Azahar suka tafi malam yayi musu Sha Tara ta arziki. Kayan malam yace suje su duba su gani saboda da an jima za'a Mika musu can gidan Alhajin. Kaya ne na gani na fada an zubasu Kamar ba gobe, an shigarwa da iya Abu ciki ta gani malam yace ta turawa makotanta na kusa suzo su gani anjima za'a Mika musu. Bayan fitowa daga sallar la'asar ne Malam Bukar ya fadawa Alhaji yanzu su malam Mudi da Alaramma malam Haruna zasu kawo kayan Zahara'u. Fada Alhajin yayi akan kayan da za'a kawo Yana fadar "Haba malam Dan me za'ayi min haka ko wancen da aka fasa auren Kai sheda ne ban karbi lefe ba da suka matsa cewa nayi suje da kayan idan tazo saiya ba matarsa". Kai malam yanjinjina Yana fadin "Anyi hakan Kam amma wannan shima bamu muka hada ba wannan yaron Sameeru ne ya turo dasu dazu yace gudunmawarsa ce aba Amarya" "Ikon Allah shi baya gajiya da dawainya haka daga wannan sai wance Allah ya saka da Alkhairi ya bar.zumunci na jima banga yaro mai karqmcinsa ba abin duniya Bai rufe Masa ido ba". Da yamma su sajida suna zaune suna Shira ita da Zahra da wata kawar Zahra Mujiba Nan take makotansu suna dasawa da Zahra sosai sun Kuma yi sabo sosai da Sajida tun lokacin da sake zuwa hutu da Sajidar lokacin suna makaranta. Ba zato ba tsammani Yara suka shigo da manyan jakunkuna dasu cylinder din gas, ai Zahra na ganin haka ta tashi da sauri ta nufi hanyar shigowa gidan da gudu ta karasa Kamar karamar yarinya suka rungume juna da Hameeda Kamar zasu fadi. Suna rike da hannun suka shigo ciki su Mujiba suna ta faman yi Mata sannu da zuwa, sai daga baya Salma ta shigo tana wani shankanshi Bata kula su Zahra ba Suma ba Wanda ya kula ta, directly dakin Mama ta nufa. Kamar jira ake Salma ta wuce saiga su Magaji da manyan Akwatunan lefe suna shigowa da sauri Zilai Mai aiki ta warto Babbar tabarma ta baza tana rabsa guda tana fadin "Masha Allah! Alherin Allah ya sauka. Fara Mai farar aniya sukari bakai farin banza Fatima Zahara'u 'yar Muhammadu sani, jikar hardon fulanin Mubi, Amarya gidan Mahmud Kuma uwar gidansa Alherin Allah ya Kai Miki, Mama!Ammah ku fito ga abin arziki ya sauka". Har rige-rigen fitowa a key tsakanin Mama da Salma yayin daga dakin Ammah Inna maimuna ta fito. 💋❤️ 💋❤️ AUREN HUCE HAUSHIN 💋❤️ 💋❤️ WRITTEN BY MAMAN FATIMAH PAGE NINE🔷(9) ____Akwatuna ne na garari masu tsadedden kyau har set biyu aka shigo dasu, sai wasu irin manyan jakunkuna guda uku, guda Zilai ta dinga gud tana fadin "wani kaya sai amale wane jaki. Allah ya Kara daukaki Fatima ya Dora ki akan makiyanki lallai girma sai dan girma kaga wadda ta gaji arziki gaba da baya" Inna maimuna ce ta jimko kudi ta dankawa zilai tana fadin "na fanshi jikata tunda kin koma roko". Dariya tayi tana fadin "wallahi Inna Dana iya kirarin da yafi wannan da nayi Mata. Uwar dakina murucin kan dutse ce Bata fito ba Saida ta shirya, yakuwar akan kabarice bakin cikin 'yan taushe, bikin cikinka sauro yau ga xanzaro a bene" . Ta Kara kwarara wata gudar. Da sauri Mama ma tazo ta dankawa zilai kudi tana fadin yau ai ranar farin ciki ce maza bude Mana muga karamar Arziki" Tunda aka Fara shigo da kayan Zahra tayi dakinsu tabar su Sajidar anan.Hameeda da zilai ne suke fama bude kayan suna santinsu komai na ciki Mai kyau ne ba karya duk wadda ta hado kayan 'yar gayu ce ta gani kasheni komai na ciki classic ne. Saida suka bude kowa ne akwatin duka Sha biyun. Ba abinda Inna maimuna ke maimatawa sai Masha Allah,Allah ya kade fitina yasa gurin zamane Allah ya hada arzikinsau. Duk bidirin da ake Salma na tsaye Bata taba ko tsinke a ciki ba sai cika take tana batsewa Kamar anyi Mata dole sai ta zaune a gurin. Su Sajida da Mujiba da Hameeda ne suka shigar da kayan falon Ammah. Sai da suka jerasu sannan Hameeda ta nufi dakin Mama su Kuma su Mujiba suka nufi gurin Zahra. Wata uwar harara Salma da dokawa Hameeda tafin tayi dogon tsaki tana fadin "Allah wadaran naka ya lalace yanzu ke ko kishin Kai Baki dashi Kika bige gurin jidar kayan kanwar bayanki kina wani washe Baki ke game kirki". Baki Hameedar ta murguda Mata tayi gaba tana cewa "Ina ruwanki Aunty Salma danke bakya ra'ayinta dole Nima sai nabi naki ra'ayi kowa yayi ta kansa kawai ni bana ara na yafa abinda Babu ruwana ba. Mama ce ta fito daga bed room dinta fuskarta a hade da waya a hannunta kallon Hameedar tayi "to rasa kunya b'eran tanka Dan ta fada Miki gaskiya Zaki kare Mata tana din rashin mutunci cewa nake koni Dana tsuguna na haifeki ban Isa kizo inda nake ba Saida Kika dangana da gurin kanwar uwarki". Baki Hameedar ta zumbura tayi gaba tana magana kasa -kasa. "Ai Daman za'a rina tunda Naga kin biyo Mama daki, wallahi mutum ya kiyayi gulma da munafurci in dai yansla son yaga ci gaba a rayuwarsa" Tana Gama fada ta shige uwar daki. A waya Ammqh ta Kira Aunty Hasana ta fada Mata an kawo lefen Zahra. Lokacin da tazo taga kayan ta kadu da gasken gaske, Amma dai Bata furta komai ba kada Ammah taga Kamar Bata son auren ne ko wani Abu. Sai bayan sallar magariba Mujiba tayiwa su Ammah sallama Sajida ta rakata ita Haidar din Aunty Hasana. Tun Zahra na tsammanin ganin Hameeda har ta hakura saboda dare ya fara so sai Dan Sajida har tayi barci, sai tayi Kamar ta kirata a waya saita fasa, da taga zaman yayi yawa sai ta dauko alqur'ani ta Fara karatu har Saida daya ta gota sannan tayi addu'a ta shafa. Kwantawa tayi rigingine tana tariyo rayuwartan ta baya komai ya ringa dawo Mata Kamar lokacin yake faruwa ************_ _ TUSHEN LABARIN AZARE KATAGUM L.G.A BAUCHI STATE UNGUWAR FAMFON SHANU. Yarinya ce 'yar kimanin sheKara goma Sha biyu haka, kyakykyawar gaske fara irin farin Nan Mai hade da Kamar golden yellow , idanunta dara-dara farare tas sai gashin kanta bakirkirin har gadon bayanta hancinta irin dogon Nan ne har baka bakinta Dan karami Mai dauke da 'yan jaja-jaja pink-pink din lebe, bazaka kirata doguwa sosai ba irin tsaka tsakiyar nan, jikin lublub Kamar Mai rayuwa a kasanshen sanyi komai nata Mai kyau ne Wanda idan ka kalleta saika Kara kallonta Dan Allah s.w.a yayi Mata sura Mai kyau na a gani a Kara kalla. Da sallama ta shigo cikin gida tana fadar "wash Allah Ammah wallahi na gaji wadannan littatafan sunyi nauyi da yawa inaga sai dai na kwafo time table kullum na ringa zuwa da Wanda zamuyi amfani dasu kawai". Ta fada tana kokarin Ciro jikar daga bayanta, dariya Ammah tayi tana fadin "ke dai anyi raguwa wallahi zahra ke Sam bakya da juriya jakar da Zaki Goya zuwa mota ma neman gagararki tajeyi". Kwantawa tayi saman kujera tana fadin "Allah da nauyi dauki fa kiji". Sulaiman ne ya shigo shima da tasa jakar a kafada Yana dariya. "Kai Kuma dariyar me kake?" Ammah ta tambaye shi. Zahra ya nuna Yana cigaba da dariya. Baki ta zumbura tana dira kafa tana fadar "Allaha Ammah ki rabani da Ya sulaiman Kinga tundazu yake min dariya Kuma nace ya tayani daukar jikar ya Kiya". "Wai Kai meye haka kazo kana ta dariya Kamar wani sabon kamu". Jakarsa ya jefa kusa data Zahra kafin ya zauna Yana ba Ammah labari. "Wato Ammah muna hanyar dawowa ne man motar ya Kare tunanin Malam Bala harya kawo mu gida man Bai Kare ba saboda yace ya biya gidan man yaga da layi idan yace zebi layin zamu Dade muna jiransa shine kawai ya taho, to muna zuwa wurin gidan sarki kawai man motar Nan ya Kare shine fa muka tako a kafa, ita Kuma gwanar iya son jiki ta wani shagwabe mini Wai na daukar Mata jaka na hada da tawa Kamar wani jaki, shine Dan tsabar rainin hankali Wai to na dauka zata karbi kudin gurin Abba ta biyani Kamar wani Dan dako". Tsaki Ammah tayi tana hararar Sulaiman din "wannan shine abin dariyar Kuma wallahi kayi girman kwabo da meye amfanin hada babba da yaron ba saboda taimakon ba". "A'a Ammah duka da wata biyar fa na girme mata, to Ina wani girma sa'anni muke ba gashi ajinmu daya ba da dai su Ya Sadiq ne su Aunty Janah, kuma fa duk su Hameeda kowa fa ya dauko tasa sai itace tafi kowa son jika za'a daukar Mata wa zata yiwa karatun ba kanta ba". Ya fada Yana cire safarsa. Fita Ammah tayi, ita Kuma Zahra ta shige bedroom din Ammah ba Wanda ya Kara bi takan sulaiman.wanka ta shiga tayi kafin taci abinci saboda Bata son ta makara a islamiyya Sam Bata son abinda ze taba lafiyar jikinta tunda a makarantar bokon suke sallar Azahar. Lokacin data fito tana sanye da uniform din islamiyya da Jakarta tana kokarin shiga dakin Mama ta biya Hameeda ne taga Hameedar da wani Kaya a wata leda babba ta fito tana zumburar Baki. "Ya Naga Baki shirya ba ko bazaki makarantar ba? Kinga fa yau zamu bada hadda". Mama ce ta fito daga dakin tana hararar Zahra "to uwar kinibibi bazatan ba ki Kama hanya ki wuce, ko zata ai bazaku tafi tare ba ana gqninki waye ze kalleta na nuna Miki bana son kina shige Mata amman kin kasa ganewa, Haba yarinya sai kwawa" Duk wanna maganar da Mama takeyi a hankali take fada Banda Zahrar da Hameedar ba Mai jin abinda take fada duk da Ammah na kofar kitchen dinsu Wanda yake kusa da bangaren na Mama. Daki Mama ta nunawa Hameeda ta koma yayin da Zahra ta nufi Ammah tana fadin "Ammah na tafi" "To Allah ya bada sa'a a maida hankali ki biyawa Mujiba ki tafi". "To" ta amsa ta nufi waje da sauri. Saida dama Ammah tana ankare da Mama Sam Bata son Zahra na mu'amala da Hameeda kwata-kwata sai Kuma Allah ya hada wata irin kauna tsakanin yaran salma ce Sam basa jituwa da Zahra da ita wata sakarai ce da zahra ko ruwa Mai dadi Salma bazata Bari Tasha a gidan ba, motsi ba motsi ba sai ta Fara fadin ai dai Nan ba gidanki bane ke 'yar riko ce. Lokacin da Ammah taji maganar a bakin yarinyar tayi mamaki sosai Dan a lokacin wayonta Bai Kai ta iya banbance tsakanin Dan gida na ruko. Da Ammah ta tsareta ta fada Mata wayace Zahra ba 'yar gidan bace sai tace " Mama ce ta fada tace min na duba Mana Naga ko kalar jiki mu ba iri daya bace mu daina tafiya ma da ita, Wai ta fimu kyau idan muna binta idan muka girma baza'a sure mu ba". Kan Salma Ammah ta dafa tana fadin "itama 'yar uwarku ce kuyi zumunci da ita kinji" kai ta gyada alamar to. Abin ya jima Yana baiwa Ammah mamaki Bata zaci haka a gurin mamar ba, tunda a zahiri ba komai a tsakaninsu sai mutunta juna duk da tasan sha'anin kishi ta ciki na ciki ne ta baka na baka. Sai kusan magariba su zahra suka shigo hannunsu na sarkafe da juna ita da Hameedar, daga gurin Aiken ta wuce makarantar Amma Tasha bulalar makara. Bayan sun Gama cin abincin dare ne suna hira a dakin Ammah Hameeda ta shigo ta gaishe da Ammah ta zauna sukaci gaba da hira lokacin Ammar tana dakin Abbansu ta Kai Masa abinci. Lokacin data shigo dakin ya kacame sunata musu akan wani aiki da akayi musu yau a makaranta su matan suna ga yanda za'ayi shi Kuma Sulaiman Yana fadar ga yanda za'ayi, Ammar ce ta zauna tana fadin su kawo ta gani maths ne, Kuma duk hanyar da akabi za'a kaiga samun amsar Dan haka tace kowa yayi nasa yanda ya fashimta. Har ta shiga bedroom dinta ta fito tana fadin "Na manta Abbanku yace na fada muku ranar Saturday zakiyi jarabawar share fagen shiga karamar secondary school ta kwamnatin tarayya, yace kuyi karatu duk Wanda baici ba baze saimasa ba Saida yaci gaba a makarantar da yake". Murna suka farayi da gudu Hameeda ta nufi dakinsu Dan ta fadawa Mama. ******Alhaji Jafar Mai yadi haifaffan garin Azare ne ta jihar Bauch a unguwar fanfon shanu, su hudu ne iyayensu suka Haifa uku maza sai autarsu daya mace amman su biyu suka rayu biyu tun suna Yara suka rasu, sun taso shi da kanwarsa Amina a hannun Babarsu Hajiya Fatima wadda ake kiranta da Nanna, kasancewar Babansu Malam Ibrahim Wanda ake Masa laqabi khalilu Allah yayi masa rasuwa tun Yana aji day na babbar sakandire Amina Kuma tana aji shida na primary. Sun Sha wahala kasancewar mahaifan su ba Mai karfi bane Bai bar musu wani Abu Mai yawa ba daga gidan da suke cikin sai konaki biyu, tunda Jafar ya Gama babbar sakandire yake zaune a gida saidai dinkin hula da aikin hannu na riguna kusan dashi yake rike Nanna da Amina said Kuma 'yan kulle-kullen kayan Miya daaya kafawa Nanna jarinsu. A hankali Jafar yana Tara kudinsa lokacin daya da yaga kudin sun danyi auki ya nemi Shawarar Nanna akan yana son ya Fara sayar da Yadiddika na maza, tayi murna sosai ta dinga saka Masa albarka. Cikin ikon Allah ya Fara kasuwar da kafar dama Nan da Nan abun ya Fara bunkasa da taimakon wani uban gida da Allah ya hada jininsu yake bashi Kaya akan farashi Mai sauki har takai ga Fara tura shi aba Yana sawo Masa Kaya a hankali ya bashi aron kudi masu Dan yawa yace shima ya hada da nasa jarin ya sawo nasa kayan zeyi Masa kokarin shago kafin ya dawo. Nan da Nan al'amura suka kankama ba'a rufe shekara ba arzikinsau ya Fara habaka da taimakon Ubangidansa ya samu Yara masu amana ya zuba a shagon shi Kuma ya shiga cuku- cukun nema admission Nan University ta Bauchi cikin ikon Allah ya samu course din da ya nema Agricultural science. Cikin ikon Allah karatu ya kankama, yayin da a gefe ga kasuwanci Yana ta habaka. Lokacin Yana shiga level 300 lokaci Amina ta kammala secondary dinta manema sukayi Mata chaaaa, Amma an kada an raya ta fitar da gwani ta Kiya Wai duk Bata sonsu. Haha aka tattara aka kyaleta Jafar yaso ya nemar Mata gurbin karatun N.C.E Amma Nanna tayi tsalle ta dire ba za'a wannan aiki da ita ba, haka suka zauna har kusan shekara Amina ita ba karatun ba ba auren ba. Wata ranar juma'a lokacin su Jafar sunzo hutun karshen first semester na level 400, Nanna ta aiki Amina kasuwa gurin Jafar ta karbo Mata wasu kudi uzurinsu ya taso Mata na gaggawa. Lokacin da taje baya shogon nasa Yana shagon Ubangidansa Alhaji Dauda, can ta nufa tunda tasan shagon nasa. Suna ciki Hira da bakon Alhaji Dauda kawai ya hango Amina ta nufo shagon tana gaishe da Alhajin daya fita a lokacin, kafin ta karaso har taso ya nufo ta Yana fadin"lafiya Amina? Daga Ina kike?" Dariya tayi kyawawan hakoranta jerarru farare tas suka bayyana tana fadin "kai Yaya ba komai fa Nanna ce ta Aiko ni". Fita sukayi ta fada Masa sakon sukaje shago ya Bata ai Bari ta hau abin Hawa ba ya dauketa a mashin dinsa suka tafi gida. Da dare Yana zaune a inda suke Hira yaga motar Alhaji Dauda ta tsaya a kofar gidansu da sauri ya tashi ya nufi inda yayi parking sai yaga harda bakon Alhajin Zakariyya suke tare, sun gaisa sosai kafin Alhaji Daudan ya fada Masa Amininsa Kuma Dan uwansa ne yaga Amina Yana so shine nace yazo muji da zafi -zafi akan bugi karfe. Jafar yaji Dadi sosai zaifi kowa murna idan hakan ta kasance Dan ya yaba sosai da hankalinsa sosai. Cikin gidan Jafar ya shiga ba jimawa ya fito Yana musu iso ciki sun gaisa da Nanna Alhaji Dauda ne yayiwa Nanna bayanin koma itama irin amsar Jafar ta fada idan tana so ba matsala ba inda aure baya Kai mace Nasarawa batayi nisa ba. Cikin ikon Allah kuwa Amina taji Alhaji Zakariyya ya kwanta mata a rai Kuma zata iya aurensa duk da fada Mata Yana da Mata harda Yara biyu. A cikin wata biyu akayi bikin Amina da Alhaji zakariyyan, Jafar yayi Mata komai da uba yake aka kaita can Nasarawa state cikin garin Akwanga. Wannan kenan. Haka Jafar yaci gaba da karatunsa har ya Gama ya dawo gida Yana jiran shiga camp. Lokacin da saki post na tafiya service sunan Jafar ya Fado a cikin masu zuwa Jos yayi murna sosai ko banza Yana jiyo kamshin gida tunda suna makotan jahohi. Bayan gama zaman camp wata makarantar 'yan Mata jeka ka dawo aka Kai Jafar, Baiyi wata biyu ba Allah ya hada shi da wata yarinya Rabi'a yaji yarinyar ta kwanta Masa tana Kuma da irin Qualities din da yake fatan Samu a gurin matarsa. Zuwa lokacin gama service dinsu har magana tayi karfi inda iyaye suka shiga. Wani gida Jafar ya saya kusa da gidansu ya gyara' ba'a dauki lokaci ba akayi bikinsa da Rabi'a suka tare a gidansu. Duk wata kulawarsa da soyayya ya tattara ya baiwa Rabi'a ba abinda ta nema ta rasa sai abinda baza'a rasa ba. Rabi'a irin matan Nan ne masu kissa kafin wani lokaci ta kanainaye zuciyar Nanna. Kwanci tashi ba wahala a gurin Allah aurensu ya shekara Amma kalubaken da suka Fara fuskanta na Rashn zaman ciki a jikin Rabi'a kusan barinta uku. Ana haka Jafar ya samu aiki da ma'aikatar gona ta jihar Bauchi BARDA. Cikin kankanin lokaci kofofin wadata suka budewa Jafar kafin shekara biyu ya gina gida Mai kyau sunje makka shida Nanna. Nan da Nan likafa tayi gaba Amma dai matsalar su na Nan ta rashin haihuwa. Yayin da abin ma ya Fara damun Nanna har ta gaji tayi Masa magana akan ko maganin hausa za'a fata nemawa Rabi'a ne. Amma sai ya nuna Mata ayi hakuri tunda tana ganin consultant na Gynicology a gani idan ba wani cigaba sai ayi na hausan. A Kuma ciki shekarar ne Alhaji Jafar ya koma Abuja da aiki inda arzikinsa ya Kara bunkasa gashi Allah yayi shi Mai sakakken hannu bashi da rowa ko kadan, in dai Yana gari to kofar gidansa Cike take da jama'a, sai Suma mutane suna tausaya Masa akan rashin haihuwa ga dukiyar dai Kama hankadota ake Amma ba magaji. Ana haka Allah ya kawo ibtila'in ambaliyar ruwa a Adamawa state yankin MUBI. Lokacin da gwamnati tarayya zata tura masu zuwa jaje sai sunan Alhaji Jafar ya shigo cikin tawagar vice president. Sun jajje guraren da b'arnar ta afku anyi rubuce rubuce sosai da Alkawarin ka na gwamnatin tarayya sanan an bada kayan agaji ga wadanda iftila'in ya shafa a hanyarsu ta komawa ne Alhaji Jafar suna tattaunawa da Ardon filanin Yana Karayi Masa bayanin abinda ya faru. Suka jiyo maganar mace daga bayansu lokacin ayarin sun danyi nisa dasu, da sauri Ardon ya juya Yama fadin "ho! 'yar nema Saida Kika biyoni Nan ko ma'u?" Dariya tayi tana kare fuskarta da wani littafin Mai Dan fadi dake hannunta cikin shiga take ta Kamala Riga da siket na lace brown sai takalman ta da jaka da mayafinta farare. Har kasa ta tsuguna tana gaishe da Baffan nata kafin ta Dan kalli gurin da Alhaji Jafar yake ta gaishe shi. Baffan nata ta mikawa littafin hannunta tana fadar "Baffa ga project din nawa komai ya kammala". Baki sake Alhaji Jafar ke kallonsu wannan 'yar yarinyar har ta Gama karatu ake nufi ko me" 💋❤️ 💋❤️ AUREN HUCE HAUSHIN 💋❤️ 💋❤️ WRITTEN BY MAMAN FATIMAH PAGE NINE🔷(9) ____Akwatuna ne na garari masu tsadedden kyau har set biyu aka shigo dasu, sai wasu irin manyan jakunkuna guda uku, guda Zilai ta dinga gud tana fadin "wani kaya sai amale wane jaki. Allah ya Kara daukaki Fatima ya Dora ki akan makiyanki lallai girma sai dan girma kaga wadda ta gaji arziki gaba da baya" Inna maimuna ce ta jimko kudi ta dankawa zilai tana fadin "na fanshi jikata tunda kin koma roko". Dariya tayi tana fadin "wallahi Inna Dana iya kirarin da yafi wannan da nayi Mata. Uwar dakina murucin kan dutse ce Bata fito ba Saida ta shirya, yakuwar akan kabarice bakin cikin 'yan taushe, bikin cikinka sauro yau ga xanzaro a bene" . Ta Kara kwarara wata gudar. Da sauri Mama ma tazo ta dankawa zilai kudi tana fadin yau ai ranar farin ciki ce maza bude Mana muga karamar Arziki" Tunda aka Fara shigo da kayan Zahra tayi dakinsu tabar su Sajidar anan.Hameeda da zilai ne suke fama bude kayan suna santinsu komai na ciki Mai kyau ne ba karya duk wadda ta hado kayan 'yar gayu ce ta gani kasheni komai na ciki classic ne. Saida suka bude kowa ne akwatin duka Sha biyun. Ba abinda Inna maimuna ke maimatawa sai Masha Allah,Allah ya kade fitina yasa gurin zamane Allah ya hada arzikinsau. Duk bidirin da ake Salma na tsaye Bata taba ko tsinke a ciki ba sai cika take tana batsewa Kamar anyi Mata dole sai ta zaune a gurin. Su Sajida da Mujiba da Hameeda ne suka shigar da kayan falon Ammah. Sai da suka jerasu sannan Hameeda ta nufi dakin Mama su Kuma su Mujiba suka nufi gurin Zahra. Wata uwar harara Salma da dokawa Hameeda tafin tayi dogon tsaki tana fadin "Allah wadaran naka ya lalace yanzu ke ko kishin Kai Baki dashi Kika bige gurin jidar kayan kanwar bayanki kina wani washe Baki ke game kirki". Baki Hameedar ta murguda Mata tayi gaba tana cewa "Ina ruwanki Aunty Salma danke bakya ra'ayinta dole Nima sai nabi naki ra'ayi kowa yayi ta kansa kawai ni bana ara na yafa abinda Babu ruwana ba. Mama ce ta fito daga bed room dinta fuskarta a hade da waya a hannunta kallon Hameedar tayi "to rasa kunya b'eran tanka Dan ta fada Miki gaskiya Zaki kare Mata tana din rashin mutunci cewa nake koni Dana tsuguna na haifeki ban Isa kizo inda nake ba Saida Kika dangana da gurin kanwar uwarki". Baki Hameedar ta zumbura tayi gaba tana magana kasa -kasa. "Ai Daman za'a rina tunda Naga kin biyo Mama daki, wallahi mutum ya kiyayi gulma da munafurci in dai yansla son yaga ci gaba a rayuwarsa" Tana Gama fada ta shige uwar daki. A waya Ammqh ta Kira Aunty Hasana ta fada Mata an kawo lefen Zahra. Lokacin da tazo taga kayan ta kadu da gasken gaske, Amma dai Bata furta komai ba kada Ammah taga Kamar Bata son auren ne ko wani Abu. Sai bayan sallar magariba Mujiba tayiwa su Ammah sallama Sajida ta rakata ita Haidar din Aunty Hasana. Tun Zahra na tsammanin ganin Hameeda har ta hakura saboda dare ya fara so sai Dan Sajida har tayi barci, sai tayi Kamar ta kirata a waya saita fasa, da taga zaman yayi yawa sai ta dauko alqur'ani ta Fara karatu har Saida daya ta gota sannan tayi addu'a ta shafa. Kwantawa tayi rigingine tana tariyo rayuwartan ta baya komai ya ringa dawo Mata Kamar lokacin yake faruwa ************_ _ TUSHEN LABARIN AZARE KATAGUM L.G.A BAUCHI STATE UNGUWAR FAMFON SHANU. Yarinya ce 'yar kimanin sheKara goma Sha biyu haka, kyakykyawar gaske fara irin farin Nan Mai hade da Kamar golden yellow , idanunta dara-dara farare tas sai gashin kanta bakirkirin har gadon bayanta hancinta irin dogon Nan ne har baka bakinta Dan karami Mai dauke da 'yan jaja-jaja pink-pink din lebe, bazaka kirata doguwa sosai ba irin tsaka tsakiyar nan, jikin lublub Kamar Mai rayuwa a kasanshen sanyi komai nata Mai kyau ne Wanda idan ka kalleta saika Kara kallonta Dan Allah s.w.a yayi Mata sura Mai kyau na a gani a Kara kalla. Da sallama ta shigo cikin gida tana fadar "wash Allah Ammah wallahi na gaji wadannan littatafan sunyi nauyi da yawa inaga sai dai na kwafo time table kullum na ringa zuwa da Wanda zamuyi amfani dasu kawai". Ta fada tana kokarin Ciro jikar daga bayanta, dariya Ammah tayi tana fadin "ke dai anyi raguwa wallahi zahra ke Sam bakya da juriya jakar da Zaki Goya zuwa mota ma neman gagararki tajeyi". Kwantawa tayi saman kujera tana fadin "Allah da nauyi dauki fa kiji". Sulaiman ne ya shigo shima da tasa jakar a kafada Yana dariya. "Kai Kuma dariyar me kake?" Ammah ta tambaye shi. Zahra ya nuna Yana cigaba da dariya. Baki ta zumbura tana dira kafa tana fadar "Allaha Ammah ki rabani da Ya sulaiman Kinga tundazu yake min dariya Kuma nace ya tayani daukar jikar ya Kiya". "Wai Kai meye haka kazo kana ta dariya Kamar wani sabon kamu". Jakarsa ya jefa kusa data Zahra kafin ya zauna Yana ba Ammah labari. "Wato Ammah muna hanyar dawowa ne man motar ya Kare tunanin Malam Bala harya kawo mu gida man Bai Kare ba saboda yace ya biya gidan man yaga da layi idan yace zebi layin zamu Dade muna jiransa shine kawai ya taho, to muna zuwa wurin gidan sarki kawai man motar Nan ya Kare shine fa muka tako a kafa, ita Kuma gwanar iya son jiki ta wani shagwabe mini Wai na daukar Mata jaka na hada da tawa Kamar wani jaki, shine Dan tsabar rainin hankali Wai to na dauka zata karbi kudin gurin Abba ta biyani Kamar wani Dan dako". Tsaki Ammah tayi tana hararar Sulaiman din "wannan shine abin dariyar Kuma wallahi kayi girman kwabo da meye amfanin hada babba da yaron ba saboda taimakon ba". "A'a Ammah duka da wata biyar fa na girme mata, to Ina wani girma sa'anni muke ba gashi ajinmu daya ba da dai su Ya Sadiq ne su Aunty Janah, kuma fa duk su Hameeda kowa fa ya dauko tasa sai itace tafi kowa son jika za'a daukar Mata wa zata yiwa karatun ba kanta ba". Ya fada Yana cire safarsa. Fita Ammah tayi, ita Kuma Zahra ta shige bedroom din Ammah ba Wanda ya Kara bi takan sulaiman.wanka ta shiga tayi kafin taci abinci saboda Bata son ta makara a islamiyya Sam Bata son abinda ze taba lafiyar jikinta tunda a makarantar bokon suke sallar Azahar. Lokacin data fito tana sanye da uniform din islamiyya da Jakarta tana kokarin shiga dakin Mama ta biya Hameeda ne taga Hameedar da wani Kaya a wata leda babba ta fito tana zumburar Baki. "Ya Naga Baki shirya ba ko bazaki makarantar ba? Kinga fa yau zamu bada hadda". Mama ce ta fito daga dakin tana hararar Zahra "to uwar kinibibi bazatan ba ki Kama hanya ki wuce, ko zata ai bazaku tafi tare ba ana gqninki waye ze kalleta na nuna Miki bana son kina shige Mata amman kin kasa ganewa, Haba yarinya sai kwawa" Duk wanna maganar da Mama takeyi a hankali take fada Banda Zahrar da Hameedar ba Mai jin abinda take fada duk da Ammah na kofar kitchen dinsu Wanda yake kusa da bangaren na Mama. Daki Mama ta nunawa Hameeda ta koma yayin da Zahra ta nufi Ammah tana fadin "Ammah na tafi" "To Allah ya bada sa'a a maida hankali ki biyawa Mujiba ki tafi". "To" ta amsa ta nufi waje da sauri. Saida dama Ammah tana ankare da Mama Sam Bata son Zahra na mu'amala da Hameeda kwata-kwata sai Kuma Allah ya hada wata irin kauna tsakanin yaran salma ce Sam basa jituwa da Zahra da ita wata sakarai ce da zahra ko ruwa Mai dadi Salma bazata Bari Tasha a gidan ba, motsi ba motsi ba sai ta Fara fadin ai dai Nan ba gidanki bane ke 'yar riko ce. Lokacin da Ammah taji maganar a bakin yarinyar tayi mamaki sosai Dan a lokacin wayonta Bai Kai ta iya banbance tsakanin Dan gida na ruko. Da Ammah ta tsareta ta fada Mata wayace Zahra ba 'yar gidan bace sai tace " Mama ce ta fada tace min na duba Mana Naga ko kalar jiki mu ba iri daya bace mu daina tafiya ma da ita, Wai ta fimu kyau idan muna binta idan muka girma baza'a sure mu ba". Kan Salma Ammah ta dafa tana fadin "itama 'yar uwarku ce kuyi zumunci da ita kinji" kai ta gyada alamar to. Abin ya jima Yana baiwa Ammah mamaki Bata zaci haka a gurin mamar ba, tunda a zahiri ba komai a tsakaninsu sai mutunta juna duk da tasan sha'anin kishi ta ciki na ciki ne ta baka na baka. Sai kusan magariba su zahra suka shigo hannunsu na sarkafe da juna ita da Hameedar, daga gurin Aiken ta wuce makarantar Amma Tasha bulalar makara. Bayan sun Gama cin abincin dare ne suna hira a dakin Ammah Hameeda ta shigo ta gaishe da Ammah ta zauna sukaci gaba da hira lokacin Ammar tana dakin Abbansu ta Kai Masa abinci. Lokacin data shigo dakin ya kacame sunata musu akan wani aiki da akayi musu yau a makaranta su matan suna ga yanda za'ayi shi Kuma Sulaiman Yana fadar ga yanda za'ayi, Ammar ce ta zauna tana fadin su kawo ta gani maths ne, Kuma duk hanyar da akabi za'a kaiga samun amsar Dan haka tace kowa yayi nasa yanda ya fashimta. Har ta shiga bedroom dinta ta fito tana fadin "Na manta Abbanku yace na fada muku ranar Saturday zakiyi jarabawar share fagen shiga karamar secondary school ta kwamnatin tarayya, yace kuyi karatu duk Wanda baici ba baze saimasa ba Saida yaci gaba a makarantar da yake". Murna suka farayi da gudu Hameeda ta nufi dakinsu Dan ta fadawa Mama. ******Alhaji Jafar Mai yadi haifaffan garin Azare ne ta jihar Bauch a unguwar fanfon shanu, su hudu ne iyayensu suka Haifa uku maza sai autarsu daya mace amman su biyu suka rayu biyu tun suna Yara suka rasu, sun taso shi da kanwarsa Amina a hannun Babarsu Hajiya Fatima wadda ake kiranta da Nanna, kasancewar Babansu Malam Ibrahim Wanda ake Masa laqabi khalilu Allah yayi masa rasuwa tun Yana aji day na babbar sakandire Amina Kuma tana aji shida na primary. Sun Sha wahala kasancewar mahaifan su ba Mai karfi bane Bai bar musu wani Abu Mai yawa ba daga gidan da suke cikin sai konaki biyu, tunda Jafar ya Gama babbar sakandire yake zaune a gida saidai dinkin hula da aikin hannu na riguna kusan dashi yake rike Nanna da Amina said Kuma 'yan kulle-kullen kayan Miya daaya kafawa Nanna jarinsu. A hankali Jafar yana Tara kudinsa lokacin daya da yaga kudin sun danyi auki ya nemi Shawarar Nanna akan yana son ya Fara sayar da Yadiddika na maza, tayi murna sosai ta dinga saka Masa albarka. Cikin ikon Allah ya Fara kasuwar da kafar dama Nan da Nan abun ya Fara bunkasa da taimakon wani uban gida da Allah ya hada jininsu yake bashi Kaya akan farashi Mai sauki har takai ga Fara tura shi aba Yana sawo Masa Kaya a hankali ya bashi aron kudi masu Dan yawa yace shima ya hada da nasa jarin ya sawo nasa kayan zeyi Masa kokarin shago kafin ya dawo. Nan da Nan al'amura suka kankama ba'a rufe shekara ba arzikinsau ya Fara habaka da taimakon Ubangidansa ya samu Yara masu amana ya zuba a shagon shi Kuma ya shiga cuku- cukun nema admission Nan University ta Bauchi cikin ikon Allah ya samu course din da ya nema Agricultural science. Cikin ikon Allah karatu ya kankama, yayin da a gefe ga kasuwanci Yana ta habaka. Lokacin Yana shiga level 300 lokaci Amina ta kammala secondary dinta manema sukayi Mata chaaaa, Amma an kada an raya ta fitar da gwani ta Kiya Wai duk Bata sonsu. Haha aka tattara aka kyaleta Jafar yaso ya nemar Mata gurbin karatun N.C.E Amma Nanna tayi tsalle ta dire ba za'a wannan aiki da ita ba, haka suka zauna har kusan shekara Amina ita ba karatun ba ba auren ba. Wata ranar juma'a lokacin su Jafar sunzo hutun karshen first semester na level 400, Nanna ta aiki Amina kasuwa gurin Jafar ta karbo Mata wasu kudi uzurinsu ya taso Mata na gaggawa. Lokacin da taje baya shogon nasa Yana shagon Ubangidansa Alhaji Dauda, can ta nufa tunda tasan shagon nasa. Suna ciki Hira da bakon Alhaji Dauda kawai ya hango Amina ta nufo shagon tana gaishe da Alhajin daya fita a lokacin, kafin ta karaso har taso ya nufo ta Yana fadin"lafiya Amina? Daga Ina kike?" Dariya tayi kyawawan hakoranta jerarru farare tas suka bayyana tana fadin "kai Yaya ba komai fa Nanna ce ta Aiko ni". Fita sukayi ta fada Masa sakon sukaje shago ya Bata ai Bari ta hau abin Hawa ba ya dauketa a mashin dinsa suka tafi gida. Da dare Yana zaune a inda suke Hira yaga motar Alhaji Dauda ta tsaya a kofar gidansu da sauri ya tashi ya nufi inda yayi parking sai yaga harda bakon Alhajin Zakariyya suke tare, sun gaisa sosai kafin Alhaji Daudan ya fada Masa Amininsa Kuma Dan uwansa ne yaga Amina Yana so shine nace yazo muji da zafi -zafi akan bugi karfe. Jafar yaji Dadi sosai zaifi kowa murna idan hakan ta kasance Dan ya yaba sosai da hankalinsa sosai. Cikin gidan Jafar ya shiga ba jimawa ya fito Yana musu iso ciki sun gaisa da Nanna Alhaji Dauda ne yayiwa Nanna bayanin koma itama irin amsar Jafar ta fada idan tana so ba matsala ba inda aure baya Kai mace Nasarawa batayi nisa ba. Cikin ikon Allah kuwa Amina taji Alhaji Zakariyya ya kwanta mata a rai Kuma zata iya aurensa duk da fada Mata Yana da Mata harda Yara biyu. A cikin wata biyu akayi bikin Amina da Alhaji zakariyyan, Jafar yayi Mata komai da uba yake aka kaita can Nasarawa state cikin garin Akwanga. Wannan kenan. Haka Jafar yaci gaba da karatunsa har ya Gama ya dawo gida Yana jiran shiga camp. Lokacin da saki post na tafiya service sunan Jafar ya Fado a cikin masu zuwa Jos yayi murna sosai ko banza Yana jiyo kamshin gida tunda suna makotan jahohi. Bayan gama zaman camp wata makarantar 'yan Mata jeka ka dawo aka Kai Jafar, Baiyi wata biyu ba Allah ya hada shi da wata yarinya Rabi'a yaji yarinyar ta kwanta Masa tana Kuma da irin Qualities din da yake fatan Samu a gurin matarsa. Zuwa lokacin gama service dinsu har magana tayi karfi inda iyaye suka shiga. Wani gida Jafar ya saya kusa da gidansu ya gyara' ba'a dauki lokaci ba akayi bikinsa da Rabi'a suka tare a gidansu. Duk wata kulawarsa da soyayya ya tattara ya baiwa Rabi'a ba abinda ta nema ta rasa sai abinda baza'a rasa ba. Rabi'a irin matan Nan ne masu kissa kafin wani lokaci ta kanainaye zuciyar Nanna. Kwanci tashi ba wahala a gurin Allah aurensu ya shekara Amma kalubaken da suka Fara fuskanta na Rashn zaman ciki a jikin Rabi'a kusan barinta uku. Ana haka Jafar ya samu aiki da ma'aikatar gona ta jihar Bauchi BARDA. Cikin kankanin lokaci kofofin wadata suka budewa Jafar kafin shekara biyu ya gina gida Mai kyau sunje makka shida Nanna. Nan da Nan likafa tayi gaba Amma dai matsalar su na Nan ta rashin haihuwa. Yayin da abin ma ya Fara damun Nanna har ta gaji tayi Masa magana akan ko maganin hausa za'a fata nemawa Rabi'a ne. Amma sai ya nuna Mata ayi hakuri tunda tana ganin consultant na Gynicology a gani idan ba wani cigaba sai ayi na hausan. A Kuma ciki shekarar ne Alhaji Jafar ya koma Abuja da aiki inda arzikinsa ya Kara bunkasa gashi Allah yayi shi Mai sakakken hannu bashi da rowa ko kadan, in dai Yana gari to kofar gidansa Cike take da jama'a, sai Suma mutane suna tausaya Masa akan rashin haihuwa ga dukiyar dai Kama hankadota ake Amma ba magaji. Ana haka Allah ya kawo ibtila'in ambaliyar ruwa a Adamawa state yankin MUBI. Lokacin da gwamnati tarayya zata tura masu zuwa jaje sai sunan Alhaji Jafar ya shigo cikin tawagar vice president. Sun jajje guraren da b'arnar ta afku anyi rubuce rubuce sosai da Alkawarin ka na gwamnatin tarayya sanan an bada kayan agaji ga wadanda iftila'in ya shafa a hanyarsu ta komawa ne Alhaji Jafar suna tattaunawa da Ardon filanin Yana Karayi Masa bayanin abinda ya faru. Suka jiyo maganar mace daga bayansu lokacin ayarin sun danyi nisa dasu, da sauri Ardon ya juya Yama fadin "ho! 'yar nema Saida Kika biyoni Nan ko ma'u?" Dariya tayi tana kare fuskarta da wani littafin Mai Dan fadi dake hannunta cikin shiga take ta Kamala Riga da siket na lace brown sai takalman ta da jaka da mayafinta farare. Har kasa ta tsuguna tana gaishe da Baffan nata kafin ta Dan kalli gurin da Alhaji Jafar yake ta gaishe shi. Baffan nata ta mikawa littafin hannunta tana fadar "Baffa ga project din nawa komai ya kammala". Baki sake Alhaji Jafar ke kallonsu wannan 'yar yarinyar har ta Gama karatu ake nufi ko me" 💋❤ 💋❤️️ AUREN HUCE HAUSHIN 💋❤️ 💋❤️ 🔷PEGE TEN🔷 Story & Written By MAMAN FATIMAH ******Jujjuya littafin project din Ardo yayi, sai Kuma ya mikawa Alhaji Jafar Yana fadin "Duba ka gani Yallabai ni tunda ba ganewa zanyi ba,naji Dadi da Allah yasa aka Gama wannan karatun ba domin na saka auduga na toshe kunnuwa naba da ba'ayi karatun Nan ba, tunda Wanda yaso auren nata yace in dai zatayi karatun Nan shi ya fasa, shi Kuma Dan uwanta na wajen kanena yace karatu Babu gashi tunda tana ganewa Kuma tana so, kaga yanzu duk gurin nan namu ita me yiwa mutane Allura". Kallonta Alhaji Jafar ya karayi,sannan ya kalli Ardon Yana fadin. "Yaushe ta Fara karatun ne na ganta karama amma har ta hada diploma?" Gyara tsayuwa Ardon yayi Yana fadin "wallahi am tun tana aji hudu na furamare Dan uwanta ta kaita aji daya na sakandire tunda yayi wani zuwa suka zauna da kannen nasa yaga tana da kokari shine yace Mata idan ta Gama makarantar tana son taci gaba da karatu, shine tace Masa tana son ta Zama malamar asibiti, to tunda sukayi haka ya kudurci aniyar tsayawa akan karatunta shi yasa da akayi Mata chaaaa akan maganar aure yace Bai Hana ayi maganar aure ba. Amma ya Dora sharadin saidai idan mijin ze barta tayi karatu abinda ya gagara kenan aka fasa Amma duk yan uwanta anyi musu". "Masha Allah. Allah ya Sanya Albarka, haka ake so a rinka barin Yara Mata suna karatu barin ma na bangaren lafiyar da malaman makaranta, yanzu ba cewa kayi ita ke yiwa mutane allura ba da sauran abubuwa? To da batayi karatun ba da basai an tafi wai gurin an nema ba? Ba komai in Sha Allah zatayi auren ta Kamar kowa". Ardo ya amsa da "Allahumma Amin". Ma'un Alhajin ya kalla "Asma'u kin amince na tafi da project din naki na duba a hankali in yasa said dawo Miki dashi". Kai ta gyada alamar Eh. Sunyi sallama da Ardo tawagarsu suka wuce zuwa Yola inda zasu bi jirgi zuwa Abuja. Wannan shine silar haduwar Alhaji Jafar da Ammah, ya koma maida project da Kuma kafa gwanatinsa cikin ikon Allah suka yarjewa juna. Lokacin da magana tayi karfi Rabi'a taso tada hankalinta saida Nanna ta taushe ta da kalamai masu kwantar da hankali. Cikin kankanin lokaci akayi bikinsu. Amarya ta tare cikin ikon Allah zaman Rabi'a da Asma'u ya kasance Zama Mai tsabta. Wata uku da auren Asma'u ciki ya bullo duk masoyin Alhaji Jafar ya Taya shi murna sosai a lokacin ne Alhaji Jafar ya biyawa Rabi'a makka kusan abinda ya kwantar Mata da hankali kenan Dan ya fada Mata idan take tayi addu'a sosai akan matsalar ta. A haka rayuwa ta dunga gurguwa har cikin ya Isa haihuwa Ardo dasu Inna maimuna sun so Ma'un to koma gida zaman haihuwa Amma Nanna ta Hana tace meye amfanin ta ita in dai sai Asma'u ta koma gida. Cikin ikon Allah a wani dare nakuda ta tasowa Asma'u lokacin Alhajin Yana nan, Nan da Nan suka nufi asibiti wurin karfe biyu da rabi Amma kafin hudu Allah ya dauketa lafiya ta haifi takwaye mace da namiji. Murna gurin wannan iyalin ba magana ranar suna yaran aka bar musu sunan su sai dai su Hassan da Hasana aka daka musu. Kullum yaran suna tsakanin Rabi'a da Asma'u suka rainon 'ya'yansu. Lokacin da aka yayesu a lokacin Allah ya baiwa Rabi'a ciki itama ba'ayi wata biyu ba Asma'u ma ta Fara laulayi, cikin ikon Allah cikin Rabi'a ya zauna kusan lokaci daya suka haihu Rabi'a haifi Hamza yayin da Asma'u ta haifi Abdul Hakeem. Bayan haihwar Hamza Rabi'a Bata Kara haihuwa ba Saida Asma'u tayi maza biyu sanan Rabi'a ta haifi mace Murjanatu, bayan Murjanatu Rabi'a ta Kara haihuwar Salma sai auta Hameeda ita Kuma Asma'u ta haifi Sulaiman sai auta Musaddiq, zuwa lokacin sunansu ya bace yayin da ake gadawa Hajiya Rabi'a Mama wasu na waje suce Hajiya Mama, Hajiya Asma'u Kuma Ammah. WACECE FATIMAH ZAHRA? 'ya daya tilo ga kanin Ammah shaqiqi Muhammad Sani. Mahaifiyar Zahra Najwa Balarabiyar Jordan ce sun hadu da Muhammad Sani ne lokacin da yaje karatu kasar da farko mutunci suke da Najwa sai daga baya ya juye ya Zama soyayya har Allah ya nufesu da aure da taimakon wani malaminsu Dan kano Dan kusan ta bagarensa su Ardo wanda suke Kira Baffa ya Sani ya Kuma amince da Malam Muhammad Kabir ya Zama waliyyin Muhammad Sani a can. Lokacin da Muhammad Sani ya Gama karatu ya zauna a can yayi aiki kusan shekara biyu daga baya ya tattaro nasu ya nasu suka dawo Nigeria, lokacin Najwa nada cikin Zahra wata bakwai a lokacin Kuma Ammah na goyon Sulaiman Mama na goyon Hameeda. A Jimeta Muhammad Sani ya sayi gida saidai suje Mubi kawai suga iyayensa,ba dadewa Najwa ta haifi 'yarta Zahra wadda taci sunan mutum biyu mahaifiyar Najwa da Mahaifiyar su Ammah. Haihuwar Zahra ba dadewa Muhammad sani ya Sami aiki a Abuja karkashi minstary of internal affairs da taimakon Alhaji Jafar. Zahra nada wata biyar wani cikin ya bullo a jikin Najwa Mai wata irin masifar laulayi, Wanda ya tilasta Ammah ta dauke Zahra daga bakin nono. Lokacin da komai da dai dai ta a gurin aikin nasa ya dauki Najwa suka koma Abuja. Saida watan haihuwarta ya Kama ya kaita Mubi shi Kuma ya koma Abuja. Lokacin data haihuwa iyayenta sunzo Nigeria da kanwarta Nawwara a Karon na biyu Mahaifiyar ta taso tafiya da Zahra Ammah ta dunga magiyar abar Mata ita harda kukanta. Lokacin da suka Gama wanka Muhammad sani yazo ya tafi dasu tafiyar da har abada Basu dawo ba a hanya sukayi hadari sun bar Jos Basu karasa Abuja ba. Yan uwa da iyaye sun shiga cikin tashin hankali marar misaltuwa Ammah tayi Kika Kamar ba gobe,ta rasa Dan uwanta shakiki, ba karamin Kai ruwa Rana akayi ba kafin Ummee kakar Zahra ta hakura ta barwa Ammah Zahrar. Tunda daga lokacin Ammah ke baiwa Zahra wata irin kulawa ta musamman sai Kuma shima Mai gidan ya kwallafa ransa akan soyayyar yarinyar abinda ya haddasa tsana Mai tsanani tsakanin Mama da zahra inda ita mamar ke ganin Kamar nema ne yasa Alhaji ke kaunar Zahra, tana ganin idan Dan tana 'ya mace ne karama ai itama tana da nata kananan 'ya'yan mata Amma baya nuna kulawa akasu Kamar Zahra ko Dan tafisu kyaune tunda Babu inda ta baro uwarta. Wannan kenan. Ranar da za'ayi jarabawar share fagen shiga karamar secondary ta gwamnatin tarayya tun sassafe zu Zahra suka shirya ita da Sulaiman da Hameeda da Salma duk da Salma ta girmesu Amma yawan yi Mata repeating yasa suka taddo ta. Har sun shiga mota Bala direba na niyyar shiga Zahra ta bude ta fito da sauri ta nufi cikin gida Sulaiman Yana kiranta tayi banza dashi ta shige da gudu ta karasa dakin Ammah tana fadin "Ammah na manta kayana da Ya Hassan ya kawo min har zamu tafi na tuna". Daga toilet Ammar ta fito ta nufi bedside locker ta janyo ta mikowa Zahra ledar tare da fadar "Maza kada ku makara mana". Kai Zahra ta gyada kafin tace "Ammah ki kara yi Mana addu'a Dan Allah Ina son naci jarabawar saboda Abbana yace idan naci makarantar zemin kyautar wani Abu" "To naji maza Allah ya bada sa'a" A kofa suka hadu da Sulaiman ya biyo ta tana fadin "Na rantsa da Allah zamu tafi mu barki ba Dan Abba ya fito ba da wallahi sai dai ki fito kiga bama gidan". Kafin ya saki labulen ya juya Zahra ta Kai kofar da zata kaika compound din gidan. Masha Allah anyi jarabawa an Gama sai jiran sakamako. A haka sukaci Baga da zuwa makaranta har suka Zama common enterence a matakin jaha. Lokacin da suka dawo zaman gida lokacin ne Alhaji Jafar da kansa ya yiwa Zahra passport da visa Saida ya Gama komai sannan ya fadawa su Ammah da Mama. Godiya Ammah ta shiga jerawa Mai gidan nasu,yayin da Mama tayi shiru Kamar bazatayi magana ba sai Kuma tace "yanzu Yallabai da kanka zaka rakata ai da Koda Hasana ko Hassan ka hadasu zasu kaita ko Kuma a fadawa cen kakanninta su turo a tafi da ita ai cacar kudin Kamar yayi yawa". Daga Ammah har Alhaji Jafar din kallon Mamar suke ita dai Ammah shiru tayi yayin da Alhajin yace. Saboda ban San darajar 'ya'ya ba zan hada Yara a tafiyar uwa duniya daga Nan har Jordan na kwanta a gida hanakli kwance ko?" Kai ta gaigice tare da fadin "gani makudan kudi za'a kashe". Wani kallo yayi Mata "kada ki kawo b'araka Rabi'a duk yaran dake gabana daya na daukesu yada zan yiwa abinda na Haifa haka zan yiwa marainiyar Allah. Da Kuma kike maganar cacar kudi idan zan jera shekara Ina Kai zahra Jordan kullum ba abinda ze girgaiza a cikin abinda na mallaka". Ku tashi kuje. Lokacin da zasu tafi anyi Mata tsara sosai Dan Nanna ma kilishi tasa aka yi Mai yawa na tsaraba. Har kano su Ammah da yara sukayi musu rakiya. Lokacin da sukaje Jordan din ba karamar murna kakanninta zukayi ba Dan Babu zato suka gansu, sun Kuma Kara yabawa da cika Alkawarin Alhaji Jafar Dan da kansa yayi musu Alkawarin ze kawo musu Zahra Dan ko a waya Bai fada musu zuwansu ba,sai address dai daya taba tambaya can wani lokaci. A ranar Zahra taga zallar soyayya a gurin dangin Najwa Dan gidan cika yayi da 'yan uwa aka dasa sabon kukan rashin Najwar da kyar Abbie da Abbanta suka dinga Basu hakuri Dan ma Alhaji Jafar ba larabcin yakeji sosai ba saidai Wanda suke Jin turanci suka ringa magana dasu. Lokacin da Alhaji Jafar din ze tafi masukin daya Kama a hotel Abbie hanawa yayi duk yanda yaso zillewa kin yarda yayi dole ya amince aka sauke shi a wani part dake kusa da nasa Ummee din, Dan ba karya dukiya dai Kam akwaita Dan shi kanshi Alhajin yayi mamakin yanda ya riskesu Bai taba kawo haka suke ba lallai yasan hadin Allah ne kawai da suka bawa Muhammad sani auren 'yarsu Dan tazarar Mai nisa ce a tsakanin su. Kwanan Alhaji Jafar bakwai ya wuce Umara yayin da Ummee tayi Masa Alkawarin zasu hadu a Saudiyyar tunda zata kawo Zahrar Nan gurin iyayenta da 'yan uwa su ganta a cikin garin Madinatul Munawwara. Satinsa daya da zuwa Suma su Zahrar sukazo Saudiyyar ita da Ummeen da Aunty Nawwara. A Nan ma Saudiyyar Zahra taga gata iya gata Dan kowa Nan Nan yake da ita, Dan kanwar Ummee Hanifa sosai ta kafe sai dai a bar Mata Zahra ta tafi da ita Istanbul inda take aure Wai Bata yarda da zaman Nigeria ba. Ankai ruwa Rana da ita kafin ta hakura Dan da gaske Alhaji Jafar ya bude Mata aiki Dan cewa yayi idan irin haka za'a ringa yi bazai Kara bawo musu ita ba saidai duk Mai son ganinta taje ya ganota Kamar yanda Ummee keyi, hakuri aka ringa bashi. Saida aka Kai Zahra makka suyi kayi umara sannan suka fara Shirin baro kasar.l Sayyaya dai Zahra ta shata Dan wasu kayan sai a awon cargo akayo musu su. Sarkar gwal da warwaro zobe kuwa kirar Saudiyya da Dubai zuwa kirar Bahrain sun Kai kala goma duk dai dai size din ta sai na Ammah biyu na Hasana ma biyu shi kanshi Alhajin anyone mass goma Sha Tara ta Arziki. Ranar da zasu dawo Zahra Tasha kuka haka kakarta Ummee,har jidda sukayo musu rakiya Basu suka tafi ba sai da jirgin su Zahra ya tashi a sararin subahanahu wata'ala. Saukar safe sukayi anan suka samu Bala direban Alhaji Dan Bai fadawa kowa sun taho ba sai Balan kawai, sau da yawa idan ya fada gashi Nan a hanya hankalin Nanna baya kwanciya har sai ya iso. Lokacin da suka shigo harabar gidan suna tsayawa Zahra to garzaya cikin gida tana fadin "Ammah!!! mun dawo". Da gudu Hameeda ta fito daga part dinsu, rungume juna sukayi suna ta tsallen murna Sai jikin zahra Hameedar ke shafawa gani take kamar canza Mata Zahrar akayi. Da sauri Ammah ta fito tana "fadin wa nake gani ne haka Kamar bakin saudiyya zuwa ba notice?" Alhajin ne ya Bata amsa. "Surprised din ki mukayi ko Zahra na?. Kai ta gyada masa. Kayansu ne su Bala da Mai gadi suka Fara shigowa dasu kafin Alhajin ya nufi part dinsa na cikin gidan yayin da Ammah ta rufa Masa baya. Har yayi wanka ya shirya Mama Bata shigo ba, har ya tambayar Ammah yayi Ina Rabi'a ? Tace Masa tana ciki watakila ko barci take. Kusan kwana su Zahra sukayi tana baiwa Hameeda labarin abinda ta gani da inda sukaje a Jordan da saudiyya, wurin karfe biyu Ammah ta tashi zatayi nafila ta jiyo su suna Hira a dayan bed room dinta lokacin wuri biyu da rabi na dare, leko tace su kwanta basu san dare yayi sosai ba. Washe gari an baje tsarabar Zahra an baiwa kowa dai dai gwargwado. Amman tsarabar Hameeda daban take Dan har sarka Saida ta baiwa Hameedar. Basifi sati biyu da dawowa ba jarabarsu ta fito ta Federal inda Zahra ta samu F.G.G.C KAZAURE yayin da Sulaiman ya samu F.G.C DAURA, Hameeda F.G.C AZARE. Salma ce kawai bata samu ba a cikinsu. Sunyi murna Kuma sunyi bakin cikin rashin samun makaranta daya duk an watsa su Abban Kuma da ya Hassan sunce kowa ya tafi inda ya samu, ita Hameeda Bata da damuwa tana gida, su Kuma duka 'ya'yan Ammah duk sun fita waje danma hanyarsu daya sai an aje Zahra a karasa da Sulaiman. Ranar da zasu tafi sun Sha kuka haka suka dauko hanya malam Bala da Ya Hassan ne suka kaisu. Lokacin da aka Kai Zahra an tashi daga aji, wasu Yara House master dinsu ya kira da wata prefect yasa su Kai Zahra room din 'yan j.s one. A cikin yaran da suka Taya Zahra daukar kayane wata yarinya tace Mata "sister kizo ki zauna a kwana ta tunda ni daya ce saman gadona ba kowa". Kai kawai zahra ta gyada Mata tana ta sauke ajiyar zuciya. Ita ta taimkawa Zahra ta shirya komai a locker dinta, Saida ta Bari zahra ta HUCE daga kukan da tsaha sannan tace Mata "ni sunana Sajida Musa ni 'yar kano ce unguwar Gwammaja kefa ya sunanki?". Nan Zahra ta fada Mata komai nata tun daga Nan suke tare har suka Zama aminai komai nasu ya Zama daya banbanci su kawai Sajida na A Zahra na C. Haka sukaci gaba da rayuwa a makarantar gasu Kuma Yara masu kwazo barin zahra ga kyau ga ilimi Nan da Nan tayi suna a makarantar kafin hutu tayi popular sosai a makarantar, idan kace 'yar larabawa kowa ya santa ba Kuma Dan Babu irin jiinsin nata ba A'a farin jini ne daga Allah. Lokacin da akayi hutu Zahra ba karamar murna tayi ba Kuma cikin ikon Allah da wuri malam Bala yazo lokacin har ya dauko Sulaiman. Bayan Azahar kadan suka shiga Azare sunyi murna sosai da ganin mutanen gida Dan Sulaiman har da kuka, Nan su Hameeda suka saka gaba suna tsokana. Haka suka cigaba da karatunsu cikin amincin Allah, lokacin da sukazo hutun third term ne akayi auren Aunty Hasana aka kaita Jos, Ya Hassan Kuma Daman Yana karatunsa a Rasha. Kowa inda yake yacigaba da karatunsa Salmace Allah ya taikata ta samu shiga FGC AZAREN itama a ss1. A haka aka dunga juyawa har suka Gama secondary School dinsu suka dawo gida. Dawowarsu ba dadewa Allah ya yiwa Nanna rasuwa rashin daya taba Abbansu sosai. Dan ya Dade Yana fama da damuwa tunda a rayuwa da ita ya tashi baisan dadin uba namiji ba itace komai nasa. Ganin abin nasa Yana neman yayi yawa yasa Abokinsa bakon malamin daya sauka Nan daura gidan Nanna da almajiransa dududu Bai zaifi sa'an Alhajin ba malam Bubar ya dukufa yi Masa addu'a tare da saka Yara kanana suna Masa addu'a, cikin ikon Allah sai komai ya daidaita. Ranar wata laraba zahra ta shirya zata raka Hameeda duba Qawarta meenal gidan Dan majalissarsu Mai wakiltar su majalissar Jaha, wani material ta saka Mai ruwan sararin samaniya yayi matukar karbar jikinta haka dinki ma ya Dace da material din, simple makeup tayi ta saka turarenta Amber oud new edition na kamfanin Al haramaini. Tunda ta fito Mama ke Mata wani irin kallo Wanda har saida ta rinqa Jin ta takura kafin Hameedar ta fito. A kasa suka taka suna Hira har sulaje gidan,sun Dan jima suna Hira da marara lafiyar kasancewar breast lump ne aka cire Mata ba wani serious case bane. Lokacin da zasu tafi suka Kara komawa gurin mamanta sukayi Mata sallama suna zaune ne da a falonta kafin meenal din tayi Mata magana ta fito. Wani handsome guy ne ya shigo falon da sallama ya Dan jefa car key dinsa sama, kana ganinsa kasan hutu ya Kama jikinsa. Ciki ya shigo lokacin da Suke amsa masa sallamarsa kujera two seaters ya zauna a Kai wadda ke facing dinsu Hameedar. Gaishe shi sukayi su Duke ya amsa Yana cewa "Hameeda daman kina Nan na Dade ban ganki ba gaskiya Ina ga tun kafin na tafi Colombia fa". Dan rausayar da Kai tayi tana fadar "wallahi Kam Ya Sahal an jima Kam kune dai bakwa ganuwa Kuna uwa duniya kunyi shiru Kum barmu da zafin Kasarmu". Ta fada tana dariya. Dai dai lokacin mommyn su meenal din ta fito kallon Sahal tayi tana fadar Kai Kuma haka mukayi da Kai?" Kaisa ya Dan Sosa da key din hannunsa Yana fadi "Iam so sorry Mom kada ki damu yanzu zanje na kawo Miki in Sha Allah." Ya fada Yana mikewa da nufin tafiya Meenal tayi tsagal tana fadin "Dan Allah Ya Sahal ka tafi dasu tunda cikin garin kayi. Suka yiwa mommy sallama da godiya suka fito da leda Mai Dan girma a hannun Meenal wadda mommyn ta Basu. Har kofar gida ya kawosu suna tsayawa ya kalli Hameeda Yana fadar "Dan Allah ki bani aron sister din take Mana Kona ten minutes ne Mana". Dan murmushi tayi tana fadar. "Ka Fara yiwa Abban mu magana dai haka Naga anayi" Ita dai Zahra ciki ta wuce Dan Kamar a kan.kaya take duk ya takura Mata da wani irin kallo har a cikin mota ma saita mirror yayi sitinta tunda Hameeda ce ta zauna a seat din gaba tana Masa Hira Amman gaba daya hankalinsa yana kan Zahra. Ita dai zahra Bata San yanda suka Kare ba taga dai Lokacin da Hameedar ta shigo ta wuce dakin su. Bayan kwana biyu da zuwa gidansu Meenal da yamma su zahra sun tafi islamiyya ne baki sukazo gurin Alhaji Jafar, ya sansu farin sani daya kanin Dan majalissar su ne dayan Kuma kanin Babansu. Yayi mamakin ganinsu Saida suka gaisa ne suka bijiro da abinda ya kawo su na yiwa yaron gurin Dan uwansu Sahal kidiba yaga yarinyar gurinsa Yana so. Shine mahaifansa ya turosu ya gabatar da maganar Yana neman izininsa na Fara zuwa gurinta Shira. Alhajin yaji Dadi sosai na yanda suka zo suka memi izininsa duk da Daman sharadinsa kenan, ya Kuma nemi Jin wacece daga cikin yaran suka gada Masa zahra ce, nan ya amince musu da addu'ar Allah ya hada kawunan su. Tun daga lokacin Sahal ya Fara zuwa gurin Zahra cikin ikon Allah tayi na'am dashi Basu Dade sosai ba sukayi wata irin shakuwa ta ban mamaki duk Wanda ya kwana ya tashi a unguwar yasan irin soyayyar da sahal yakewa zahra kusan Kullum da yamma Yana nan makale da ita, a haka har manya suka shiga maganar aka tsaida lokaci wata shida inda zasu tafi Colombia inda yake hada masters dinsa ita kuma zata Fara nata degree din. Anyi lefe na garari Wanda ya dauki Baki fiye da tunanin Mai tunani, an kashe kudi Kamar ba'a San zafinsu ba. Lokacin da bikin ya rage baifi saura wata biyu ba sai lamarin ya Fara canzawa kwata -kwata Sahal ya rage zuwa gurin Zahra haka ma sai a kwana a wuni Bai kirata ba, duk wani zazzari da yake na bikin su events din da yake ta faman damun zahra da maganar duk ya daina Kai tafi-tafi sai ayi kwana uku hudu har sati Bai kirata ba, da farkon abin tana kiransa taji ko lafiya a yanayin yanda yake amsa Mata wayar saita hakura da Kiran nasa, tun Ammah na zuba ido har ta samu Zahra a wani dare ta tsareta da tambayar ko wani Abu ya hadata da Sahal ne? Ta Bata tabbacin ba abinda ya hadasu sai dai ta fada Mata yanda suka ringa yi dashi a kwanaki idan ta Kira shi. Addu'a Ammah ta Bata tace ta ringa yi itama zataci gaba da yi, Mata sannan ta umarceta da kada ta Kara kiransa a wayar ta zuba ido kawai. Duk abinda Ammah take na shirye-shiryen Baki Bata fasa ba, tayi waya mutanan Jordan ma sunce suna Nan tafe Amma a daure a turo Zahra Kamar saura wata data bikin. Ba'afi sati daya da waya da kakanninta na uwa ba sakon kayan dakinta ya sauka Nigeria daga Istanbul kayan da suka gigita Mama Dan ba kayan Wasa bane set din gado har hudu kujeru set uku bayan electronics kuwa wasu har ba'a San amfaninsu ba sai dai idan an duba manual din. Alhaji Jafar yayi fada Kamar ya Ari Baki lokacin daya Kira Abbie akan danme zasuyi Masa haka toshi meye amfaninsa da bazasu Bari yayi Mata kayan dakin ba. Hakuri Abbien ya shiga bashi akan su basuyi Dan su Bata Masa raiba, sunga abinda ya kamata suyiwa diyar Najwa kenan. Ammah da Mama Alhaji Jafar ya Kira ya fada musu tunda an Riga an yiwa zahra kayan dakin da duk abinda ya kamata to ga fifty million Nan ya baiwa Zahra idan komai ya nutsa saita Fara business na abinda take son sayarwa sannan ya Bata shanu biyar. Kuka Ammah ta saka saboda Dadi ta rasa bakin da zatayi Masa godiya, yanda take dawainya da wannan marainiyar Allah Bai taba gajiyawa ba. Mama ce ta Ari bakinta tana ta yiwa Abban godiya da saka Albarka sai faman dariya tace bakinta yaki rufuwa, tun Ammah na ganin dariyar farin ciki ce har ta Fara wani tunani na daban, Nan da Nan ta Kori shaidan akan abinda zuciya ke sawwala Mata. Lokaci na Kara tafiya daukewar ma'amala na Kara yawaita a tsakanin Sahal da zahra, yanzu ta Kai kwata-kwata sun daina waya dashi, ana saura kwana talatin da hudu a Fara biki Wanda yayi daidai da saura kwana uku zahra da Hameeda da Abdul Hakeem su tafi Istanbul. Dan direct gurin kanwar Ummeen Hanifa zasu tafi daga baya su Ummeen sun samesu a can, idan an Gama komai su rankato Nigeria Dan da gaske Ummee ta shiryawa bikin sosai. Washe gari, tunda gari ya waje Mama ke Kai kawo tsakar gida duk da ba aikinta bane ba Kuma halayyarta bane hakan. Yayin da a bangaren Ammah ta rasa me yake Mata Dadi duk kasala ta baibayeta jinta take Kamar ma zazzabi na neman rufata... 💋❤ 💋❤️️ AUREN HUCE HAUSHIN 💋❤️ 💋❤️ 🔷PEGE TEN🔷 Story & Written By MAMAN FATIMAH ******Jujjuya littafin project din Ardo yayi, sai Kuma ya mikawa Alhaji Jafar Yana fadin "Duba ka gani Yallabai ni tunda ba ganewa zanyi ba,naji Dadi da Allah yasa aka Gama wannan karatun ba domin na saka auduga na toshe kunnuwa naba da ba'ayi karatun Nan ba, tunda Wanda yaso auren nata yace in dai zatayi karatun Nan shi ya fasa, shi Kuma Dan uwanta na wajen kanena yace karatu Babu gashi tunda tana ganewa Kuma tana so, kaga yanzu duk gurin nan namu ita me yiwa mutane Allura". Kallonta Alhaji Jafar ya karayi,sannan ya kalli Ardon Yana fadin. "Yaushe ta Fara karatun ne na ganta karama amma har ta hada diploma?" Gyara tsayuwa Ardon yayi Yana fadin "wallahi am tun tana aji hudu na furamare Dan uwanta ta kaita aji daya na sakandire tunda yayi wani zuwa suka zauna da kannen nasa yaga tana da kokari shine yace Mata idan ta Gama makarantar tana son taci gaba da karatu, shine tace Masa tana son ta Zama malamar asibiti, to tunda sukayi haka ya kudurci aniyar tsayawa akan karatunta shi yasa da akayi Mata chaaaa akan maganar aure yace Bai Hana ayi maganar aure ba. Amma ya Dora sharadin saidai idan mijin ze barta tayi karatu abinda ya gagara kenan aka fasa Amma duk yan uwanta anyi musu". "Masha Allah. Allah ya Sanya Albarka, haka ake so a rinka barin Yara Mata suna karatu barin ma na bangaren lafiyar da malaman makaranta, yanzu ba cewa kayi ita ke yiwa mutane allura ba da sauran abubuwa? To da batayi karatun ba da basai an tafi wai gurin an nema ba? Ba komai in Sha Allah zatayi auren ta Kamar kowa". Ardo ya amsa da "Allahumma Amin". Ma'un Alhajin ya kalla "Asma'u kin amince na tafi da project din naki na duba a hankali in yasa said dawo Miki dashi". Kai ta gyada alamar Eh. Sunyi sallama da Ardo tawagarsu suka wuce zuwa Yola inda zasu bi jirgi zuwa Abuja. Wannan shine silar haduwar Alhaji Jafar da Ammah, ya koma maida project da Kuma kafa gwanatinsa cikin ikon Allah suka yarjewa juna. Lokacin da magana tayi karfi Rabi'a taso tada hankalinta saida Nanna ta taushe ta da kalamai masu kwantar da hankali. Cikin kankanin lokaci akayi bikinsu. Amarya ta tare cikin ikon Allah zaman Rabi'a da Asma'u ya kasance Zama Mai tsabta. Wata uku da auren Asma'u ciki ya bullo duk masoyin Alhaji Jafar ya Taya shi murna sosai a lokacin ne Alhaji Jafar ya biyawa Rabi'a makka kusan abinda ya kwantar Mata da hankali kenan Dan ya fada Mata idan take tayi addu'a sosai akan matsalar ta. A haka rayuwa ta dunga gurguwa har cikin ya Isa haihuwa Ardo dasu Inna maimuna sun so Ma'un to koma gida zaman haihuwa Amma Nanna ta Hana tace meye amfanin ta ita in dai sai Asma'u ta koma gida. Cikin ikon Allah a wani dare nakuda ta tasowa Asma'u lokacin Alhajin Yana nan, Nan da Nan suka nufi asibiti wurin karfe biyu da rabi Amma kafin hudu Allah ya dauketa lafiya ta haifi takwaye mace da namiji. Murna gurin wannan iyalin ba magana ranar suna yaran aka bar musu sunan su sai dai su Hassan da Hasana aka daka musu. Kullum yaran suna tsakanin Rabi'a da Asma'u suka rainon 'ya'yansu. Lokacin da aka yayesu a lokacin Allah ya baiwa Rabi'a ciki itama ba'ayi wata biyu ba Asma'u ma ta Fara laulayi, cikin ikon Allah cikin Rabi'a ya zauna kusan lokaci daya suka haihu Rabi'a haifi Hamza yayin da Asma'u ta haifi Abdul Hakeem. Bayan haihwar Hamza Rabi'a Bata Kara haihuwa ba Saida Asma'u tayi maza biyu sanan Rabi'a ta haifi mace Murjanatu, bayan Murjanatu Rabi'a ta Kara haihuwar Salma sai auta Hameeda ita Kuma Asma'u ta haifi Sulaiman sai auta Musaddiq, zuwa lokacin sunansu ya bace yayin da ake gadawa Hajiya Rabi'a Mama wasu na waje suce Hajiya Mama, Hajiya Asma'u Kuma Ammah. WACECE FATIMAH ZAHRA? 'ya daya tilo ga kanin Ammah shaqiqi Muhammad Sani. Mahaifiyar Zahra Najwa Balarabiyar Jordan ce sun hadu da Muhammad Sani ne lokacin da yaje karatu kasar da farko mutunci suke da Najwa sai daga baya ya juye ya Zama soyayya har Allah ya nufesu da aure da taimakon wani malaminsu Dan kano Dan kusan ta bagarensa su Ardo wanda suke Kira Baffa ya Sani ya Kuma amince da Malam Muhammad Kabir ya Zama waliyyin Muhammad Sani a can. Lokacin da Muhammad Sani ya Gama karatu ya zauna a can yayi aiki kusan shekara biyu daga baya ya tattaro nasu ya nasu suka dawo Nigeria, lokacin Najwa nada cikin Zahra wata bakwai a lokacin Kuma Ammah na goyon Sulaiman Mama na goyon Hameeda. A Jimeta Muhammad Sani ya sayi gida saidai suje Mubi kawai suga iyayensa,ba dadewa Najwa ta haifi 'yarta Zahra wadda taci sunan mutum biyu mahaifiyar Najwa da Mahaifiyar su Ammah. Haihuwar Zahra ba dadewa Muhammad sani ya Sami aiki a Abuja karkashi minstary of internal affairs da taimakon Alhaji Jafar. Zahra nada wata biyar wani cikin ya bullo a jikin Najwa Mai wata irin masifar laulayi, Wanda ya tilasta Ammah ta dauke Zahra daga bakin nono. Lokacin da komai da dai dai ta a gurin aikin nasa ya dauki Najwa suka koma Abuja. Saida watan haihuwarta ya Kama ya kaita Mubi shi Kuma ya koma Abuja. Lokacin data haihuwa iyayenta sunzo Nigeria da kanwarta Nawwara a Karon na biyu Mahaifiyar ta taso tafiya da Zahra Ammah ta dunga magiyar abar Mata ita harda kukanta. Lokacin da suka Gama wanka Muhammad sani yazo ya tafi dasu tafiyar da har abada Basu dawo ba a hanya sukayi hadari sun bar Jos Basu karasa Abuja ba. Yan uwa da iyaye sun shiga cikin tashin hankali marar misaltuwa Ammah tayi Kika Kamar ba gobe,ta rasa Dan uwanta shakiki, ba karamin Kai ruwa Rana akayi ba kafin Ummee kakar Zahra ta hakura ta barwa Ammah Zahrar. Tunda daga lokacin Ammah ke baiwa Zahra wata irin kulawa ta musamman sai Kuma shima Mai gidan ya kwallafa ransa akan soyayyar yarinyar abinda ya haddasa tsana Mai tsanani tsakanin Mama da zahra inda ita mamar ke ganin Kamar nema ne yasa Alhaji ke kaunar Zahra, tana ganin idan Dan tana 'ya mace ne karama ai itama tana da nata kananan 'ya'yan mata Amma baya nuna kulawa akasu Kamar Zahra ko Dan tafisu kyaune tunda Babu inda ta baro uwarta. Wannan kenan. Ranar da za'ayi jarabawar share fagen shiga karamar secondary ta gwamnatin tarayya tun sassafe zu Zahra suka shirya ita da Sulaiman da Hameeda da Salma duk da Salma ta girmesu Amma yawan yi Mata repeating yasa suka taddo ta. Har sun shiga mota Bala direba na niyyar shiga Zahra ta bude ta fito da sauri ta nufi cikin gida Sulaiman Yana kiranta tayi banza dashi ta shige da gudu ta karasa dakin Ammah tana fadin "Ammah na manta kayana da Ya Hassan ya kawo min har zamu tafi na tuna". Daga toilet Ammar ta fito ta nufi bedside locker ta janyo ta mikowa Zahra ledar tare da fadar "Maza kada ku makara mana". Kai Zahra ta gyada kafin tace "Ammah ki kara yi Mana addu'a Dan Allah Ina son naci jarabawar saboda Abbana yace idan naci makarantar zemin kyautar wani Abu" "To naji maza Allah ya bada sa'a" A kofa suka hadu da Sulaiman ya biyo ta tana fadin "Na rantsa da Allah zamu tafi mu barki ba Dan Abba ya fito ba da wallahi sai dai ki fito kiga bama gidan". Kafin ya saki labulen ya juya Zahra ta Kai kofar da zata kaika compound din gidan. Masha Allah anyi jarabawa an Gama sai jiran sakamako. A haka sukaci Baga da zuwa makaranta har suka Zama common enterence a matakin jaha. Lokacin da suka dawo zaman gida lokacin ne Alhaji Jafar da kansa ya yiwa Zahra passport da visa Saida ya Gama komai sannan ya fadawa su Ammah da Mama. Godiya Ammah ta shiga jerawa Mai gidan nasu,yayin da Mama tayi shiru Kamar bazatayi magana ba sai Kuma tace "yanzu Yallabai da kanka zaka rakata ai da Koda Hasana ko Hassan ka hadasu zasu kaita ko Kuma a fadawa cen kakanninta su turo a tafi da ita ai cacar kudin Kamar yayi yawa". Daga Ammah har Alhaji Jafar din kallon Mamar suke ita dai Ammah shiru tayi yayin da Alhajin yace. Saboda ban San darajar 'ya'ya ba zan hada Yara a tafiyar uwa duniya daga Nan har Jordan na kwanta a gida hanakli kwance ko?" Kai ta gaigice tare da fadin "gani makudan kudi za'a kashe". Wani kallo yayi Mata "kada ki kawo b'araka Rabi'a duk yaran dake gabana daya na daukesu yada zan yiwa abinda na Haifa haka zan yiwa marainiyar Allah. Da Kuma kike maganar cacar kudi idan zan jera shekara Ina Kai zahra Jordan kullum ba abinda ze girgaiza a cikin abinda na mallaka". Ku tashi kuje. Lokacin da zasu tafi anyi Mata tsara sosai Dan Nanna ma kilishi tasa aka yi Mai yawa na tsaraba. Har kano su Ammah da yara sukayi musu rakiya. Lokacin da sukaje Jordan din ba karamar murna kakanninta zukayi ba Dan Babu zato suka gansu, sun Kuma Kara yabawa da cika Alkawarin Alhaji Jafar Dan da kansa yayi musu Alkawarin ze kawo musu Zahra Dan ko a waya Bai fada musu zuwansu ba,sai address dai daya taba tambaya can wani lokaci. A ranar Zahra taga zallar soyayya a gurin dangin Najwa Dan gidan cika yayi da 'yan uwa aka dasa sabon kukan rashin Najwar da kyar Abbie da Abbanta suka dinga Basu hakuri Dan ma Alhaji Jafar ba larabcin yakeji sosai ba saidai Wanda suke Jin turanci suka ringa magana dasu. Lokacin da Alhaji Jafar din ze tafi masukin daya Kama a hotel Abbie hanawa yayi duk yanda yaso zillewa kin yarda yayi dole ya amince aka sauke shi a wani part dake kusa da nasa Ummee din, Dan ba karya dukiya dai Kam akwaita Dan shi kanshi Alhajin yayi mamakin yanda ya riskesu Bai taba kawo haka suke ba lallai yasan hadin Allah ne kawai da suka bawa Muhammad sani auren 'yarsu Dan tazarar Mai nisa ce a tsakanin su. Kwanan Alhaji Jafar bakwai ya wuce Umara yayin da Ummee tayi Masa Alkawarin zasu hadu a Saudiyyar tunda zata kawo Zahrar Nan gurin iyayenta da 'yan uwa su ganta a cikin garin Madinatul Munawwara. Satinsa daya da zuwa Suma su Zahrar sukazo Saudiyyar ita da Ummeen da Aunty Nawwara. A Nan ma Saudiyyar Zahra taga gata iya gata Dan kowa Nan Nan yake da ita, Dan kanwar Ummee Hanifa sosai ta kafe sai dai a bar Mata Zahra ta tafi da ita Istanbul inda take aure Wai Bata yarda da zaman Nigeria ba. Ankai ruwa Rana da ita kafin ta hakura Dan da gaske Alhaji Jafar ya bude Mata aiki Dan cewa yayi idan irin haka za'a ringa yi bazai Kara bawo musu ita ba saidai duk Mai son ganinta taje ya ganota Kamar yanda Ummee keyi, hakuri aka ringa bashi. Saida aka Kai Zahra makka suyi kayi umara sannan suka fara Shirin baro kasar.l Sayyaya dai Zahra ta shata Dan wasu kayan sai a awon cargo akayo musu su. Sarkar gwal da warwaro zobe kuwa kirar Saudiyya da Dubai zuwa kirar Bahrain sun Kai kala goma duk dai dai size din ta sai na Ammah biyu na Hasana ma biyu shi kanshi Alhajin anyone mass goma Sha Tara ta Arziki. Ranar da zasu dawo Zahra Tasha kuka haka kakarta Ummee,har jidda sukayo musu rakiya Basu suka tafi ba sai da jirgin su Zahra ya tashi a sararin subahanahu wata'ala. Saukar safe sukayi anan suka samu Bala direban Alhaji Dan Bai fadawa kowa sun taho ba sai Balan kawai, sau da yawa idan ya fada gashi Nan a hanya hankalin Nanna baya kwanciya har sai ya iso. Lokacin da suka shigo harabar gidan suna tsayawa Zahra to garzaya cikin gida tana fadin "Ammah!!! mun dawo". Da gudu Hameeda ta fito daga part dinsu, rungume juna sukayi suna ta tsallen murna Sai jikin zahra Hameedar ke shafawa gani take kamar canza Mata Zahrar akayi. Da sauri Ammah ta fito tana "fadin wa nake gani ne haka Kamar bakin saudiyya zuwa ba notice?" Alhajin ne ya Bata amsa. "Surprised din ki mukayi ko Zahra na?. Kai ta gyada masa. Kayansu ne su Bala da Mai gadi suka Fara shigowa dasu kafin Alhajin ya nufi part dinsa na cikin gidan yayin da Ammah ta rufa Masa baya. Har yayi wanka ya shirya Mama Bata shigo ba, har ya tambayar Ammah yayi Ina Rabi'a ? Tace Masa tana ciki watakila ko barci take. Kusan kwana su Zahra sukayi tana baiwa Hameeda labarin abinda ta gani da inda sukaje a Jordan da saudiyya, wurin karfe biyu Ammah ta tashi zatayi nafila ta jiyo su suna Hira a dayan bed room dinta lokacin wuri biyu da rabi na dare, leko tace su kwanta basu san dare yayi sosai ba. Washe gari an baje tsarabar Zahra an baiwa kowa dai dai gwargwado. Amman tsarabar Hameeda daban take Dan har sarka Saida ta baiwa Hameedar. Basifi sati biyu da dawowa ba jarabarsu ta fito ta Federal inda Zahra ta samu F.G.G.C KAZAURE yayin da Sulaiman ya samu F.G.C DAURA, Hameeda F.G.C AZARE. Salma ce kawai bata samu ba a cikinsu. Sunyi murna Kuma sunyi bakin cikin rashin samun makaranta daya duk an watsa su Abban Kuma da ya Hassan sunce kowa ya tafi inda ya samu, ita Hameeda Bata da damuwa tana gida, su Kuma duka 'ya'yan Ammah duk sun fita waje danma hanyarsu daya sai an aje Zahra a karasa da Sulaiman. Ranar da zasu tafi sun Sha kuka haka suka dauko hanya malam Bala da Ya Hassan ne suka kaisu. Lokacin da aka Kai Zahra an tashi daga aji, wasu Yara House master dinsu ya kira da wata prefect yasa su Kai Zahra room din 'yan j.s one. A cikin yaran da suka Taya Zahra daukar kayane wata yarinya tace Mata "sister kizo ki zauna a kwana ta tunda ni daya ce saman gadona ba kowa". Kai kawai zahra ta gyada Mata tana ta sauke ajiyar zuciya. Ita ta taimkawa Zahra ta shirya komai a locker dinta, Saida ta Bari zahra ta HUCE daga kukan da tsaha sannan tace Mata "ni sunana Sajida Musa ni 'yar kano ce unguwar Gwammaja kefa ya sunanki?". Nan Zahra ta fada Mata komai nata tun daga Nan suke tare har suka Zama aminai komai nasu ya Zama daya banbanci su kawai Sajida na A Zahra na C. Haka sukaci gaba da rayuwa a makarantar gasu Kuma Yara masu kwazo barin zahra ga kyau ga ilimi Nan da Nan tayi suna a makarantar kafin hutu tayi popular sosai a makarantar, idan kace 'yar larabawa kowa ya santa ba Kuma Dan Babu irin jiinsin nata ba A'a farin jini ne daga Allah. Lokacin da akayi hutu Zahra ba karamar murna tayi ba Kuma cikin ikon Allah da wuri malam Bala yazo lokacin har ya dauko Sulaiman. Bayan Azahar kadan suka shiga Azare sunyi murna sosai da ganin mutanen gida Dan Sulaiman har da kuka, Nan su Hameeda suka saka gaba suna tsokana. Haka suka cigaba da karatunsu cikin amincin Allah, lokacin da sukazo hutun third term ne akayi auren Aunty Hasana aka kaita Jos, Ya Hassan Kuma Daman Yana karatunsa a Rasha. Kowa inda yake yacigaba da karatunsa Salmace Allah ya taikata ta samu shiga FGC AZAREN itama a ss1. A haka aka dunga juyawa har suka Gama secondary School dinsu suka dawo gida. Dawowarsu ba dadewa Allah ya yiwa Nanna rasuwa rashin daya taba Abbansu sosai. Dan ya Dade Yana fama da damuwa tunda a rayuwa da ita ya tashi baisan dadin uba namiji ba itace komai nasa. Ganin abin nasa Yana neman yayi yawa yasa Abokinsa bakon malamin daya sauka Nan daura gidan Nanna da almajiransa dududu Bai zaifi sa'an Alhajin ba malam Bubar ya dukufa yi Masa addu'a tare da saka Yara kanana suna Masa addu'a, cikin ikon Allah sai komai ya daidaita. Ranar wata laraba zahra ta shirya zata raka Hameeda duba Qawarta meenal gidan Dan majalissarsu Mai wakiltar su majalissar Jaha, wani material ta saka Mai ruwan sararin samaniya yayi matukar karbar jikinta haka dinki ma ya Dace da material din, simple makeup tayi ta saka turarenta Amber oud new edition na kamfanin Al haramaini. Tunda ta fito Mama ke Mata wani irin kallo Wanda har saida ta rinqa Jin ta takura kafin Hameedar ta fito. A kasa suka taka suna Hira har sulaje gidan,sun Dan jima suna Hira da marara lafiyar kasancewar breast lump ne aka cire Mata ba wani serious case bane. Lokacin da zasu tafi suka Kara komawa gurin mamanta sukayi Mata sallama suna zaune ne da a falonta kafin meenal din tayi Mata magana ta fito. Wani handsome guy ne ya shigo falon da sallama ya Dan jefa car key dinsa sama, kana ganinsa kasan hutu ya Kama jikinsa. Ciki ya shigo lokacin da Suke amsa masa sallamarsa kujera two seaters ya zauna a Kai wadda ke facing dinsu Hameedar. Gaishe shi sukayi su Duke ya amsa Yana cewa "Hameeda daman kina Nan na Dade ban ganki ba gaskiya Ina ga tun kafin na tafi Colombia fa". Dan rausayar da Kai tayi tana fadar "wallahi Kam Ya Sahal an jima Kam kune dai bakwa ganuwa Kuna uwa duniya kunyi shiru Kum barmu da zafin Kasarmu". Ta fada tana dariya. Dai dai lokacin mommyn su meenal din ta fito kallon Sahal tayi tana fadar Kai Kuma haka mukayi da Kai?" Kaisa ya Dan Sosa da key din hannunsa Yana fadi "Iam so sorry Mom kada ki damu yanzu zanje na kawo Miki in Sha Allah." Ya fada Yana mikewa da nufin tafiya Meenal tayi tsagal tana fadin "Dan Allah Ya Sahal ka tafi dasu tunda cikin garin kayi. Suka yiwa mommy sallama da godiya suka fito da leda Mai Dan girma a hannun Meenal wadda mommyn ta Basu. Har kofar gida ya kawosu suna tsayawa ya kalli Hameeda Yana fadar "Dan Allah ki bani aron sister din take Mana Kona ten minutes ne Mana". Dan murmushi tayi tana fadar. "Ka Fara yiwa Abban mu magana dai haka Naga anayi" Ita dai Zahra ciki ta wuce Dan Kamar a kan.kaya take duk ya takura Mata da wani irin kallo har a cikin mota ma saita mirror yayi sitinta tunda Hameeda ce ta zauna a seat din gaba tana Masa Hira Amman gaba daya hankalinsa yana kan Zahra. Ita dai zahra Bata San yanda suka Kare ba taga dai Lokacin da Hameedar ta shigo ta wuce dakin su. Bayan kwana biyu da zuwa gidansu Meenal da yamma su zahra sun tafi islamiyya ne baki sukazo gurin Alhaji Jafar, ya sansu farin sani daya kanin Dan majalissar su ne dayan Kuma kanin Babansu. Yayi mamakin ganinsu Saida suka gaisa ne suka bijiro da abinda ya kawo su na yiwa yaron gurin Dan uwansu Sahal kidiba yaga yarinyar gurinsa Yana so. Shine mahaifansa ya turosu ya gabatar da maganar Yana neman izininsa na Fara zuwa gurinta Shira. Alhajin yaji Dadi sosai na yanda suka zo suka memi izininsa duk da Daman sharadinsa kenan, ya Kuma nemi Jin wacece daga cikin yaran suka gada Masa zahra ce, nan ya amince musu da addu'ar Allah ya hada kawunan su. Tun daga lokacin Sahal ya Fara zuwa gurin Zahra cikin ikon Allah tayi na'am dashi Basu Dade sosai ba sukayi wata irin shakuwa ta ban mamaki duk Wanda ya kwana ya tashi a unguwar yasan irin soyayyar da sahal yakewa zahra kusan Kullum da yamma Yana nan makale da ita, a haka har manya suka shiga maganar aka tsaida lokaci wata shida inda zasu tafi Colombia inda yake hada masters dinsa ita kuma zata Fara nata degree din. Anyi lefe na garari Wanda ya dauki Baki fiye da tunanin Mai tunani, an kashe kudi Kamar ba'a San zafinsu ba. Lokacin da bikin ya rage baifi saura wata biyu ba sai lamarin ya Fara canzawa kwata -kwata Sahal ya rage zuwa gurin Zahra haka ma sai a kwana a wuni Bai kirata ba, duk wani zazzari da yake na bikin su events din da yake ta faman damun zahra da maganar duk ya daina Kai tafi-tafi sai ayi kwana uku hudu har sati Bai kirata ba, da farkon abin tana kiransa taji ko lafiya a yanayin yanda yake amsa Mata wayar saita hakura da Kiran nasa, tun Ammah na zuba ido har ta samu Zahra a wani dare ta tsareta da tambayar ko wani Abu ya hadata da Sahal ne? Ta Bata tabbacin ba abinda ya hadasu sai dai ta fada Mata yanda suka ringa yi dashi a kwanaki idan ta Kira shi. Addu'a Ammah ta Bata tace ta ringa yi itama zataci gaba da yi, Mata sannan ta umarceta da kada ta Kara kiransa a wayar ta zuba ido kawai. Duk abinda Ammah take na shirye-shiryen Baki Bata fasa ba, tayi waya mutanan Jordan ma sunce suna Nan tafe Amma a daure a turo Zahra Kamar saura wata data bikin. Ba'afi sati daya da waya da kakanninta na uwa ba sakon kayan dakinta ya sauka Nigeria daga Istanbul kayan da suka gigita Mama Dan ba kayan Wasa bane set din gado har hudu kujeru set uku bayan electronics kuwa wasu har ba'a San amfaninsu ba sai dai idan an duba manual din. Alhaji Jafar yayi fada Kamar ya Ari Baki lokacin daya Kira Abbie akan danme zasuyi Masa haka toshi meye amfaninsa da bazasu Bari yayi Mata kayan dakin ba. Hakuri Abbien ya shiga bashi akan su basuyi Dan su Bata Masa raiba, sunga abinda ya kamata suyiwa diyar Najwa kenan. Ammah da Mama Alhaji Jafar ya Kira ya fada musu tunda an Riga an yiwa zahra kayan dakin da duk abinda ya kamata to ga fifty million Nan ya baiwa Zahra idan komai ya nutsa saita Fara business na abinda take son sayarwa sannan ya Bata shanu biyar. Kuka Ammah ta saka saboda Dadi ta rasa bakin da zatayi Masa godiya, yanda take dawainya da wannan marainiyar Allah Bai taba gajiyawa ba. Mama ce ta Ari bakinta tana ta yiwa Abban godiya da saka Albarka sai faman dariya tace bakinta yaki rufuwa, tun Ammah na ganin dariyar farin ciki ce har ta Fara wani tunani na daban, Nan da Nan ta Kori shaidan akan abinda zuciya ke sawwala Mata. Lokaci na Kara tafiya daukewar ma'amala na Kara yawaita a tsakanin Sahal da zahra, yanzu ta Kai kwata-kwata sun daina waya dashi, ana saura kwana talatin da hudu a Fara biki Wanda yayi daidai da saura kwana uku zahra da Hameeda da Abdul Hakeem su tafi Istanbul. Dan direct gurin kanwar Ummeen Hanifa zasu tafi daga baya su Ummeen sun samesu a can, idan an Gama komai su rankato Nigeria Dan da gaske Ummee ta shiryawa bikin sosai. Washe gari, tunda gari ya waje Mama ke Kai kawo tsakar gida duk da ba aikinta bane ba Kuma halayyarta bane hakan. Yayin da a bangaren Ammah ta rasa me yake Mata Dadi duk kasala ta baibayeta jinta take Kamar ma zazzabi na neman rufata... 💋❤ 💋❤️ ✨AUREN HUCE HAUSHIN ✨️ 💋❤️ 💋❤️ STORY & WRITTEN BY MAMAN FATIMAH. 🔷✨PAGE ELEVEN✨🔷 (11) ________Misalin Sha biyu da rabi na Rana kawar Mama kuma Aminiyar Asabe tazo gidan macece wayayya Mai kisisina Bata fiye zuwa gidan sosai ba sai lokaci lokaci, ta Dan jima a dakin Ammah suna hira har tana tsokanar zahra da Amaryar gobe ana dariya. Part din Mama ta shiga suka kule a master bedroom dinta. Batafi awa daya da zuwa ba, wasu Mata suka shigo gidan lokacin Ammah tana bangaren Abba. Zilai Mai aik cei ta leko tana fadin "uwar dakina anyi baki kuwa ko Ammah zaki yiwa magana Naga bakin nata be" Mayafi karami ta Dora a saman gashinta da tayi parking dinsa har wajen kugunta Yana reto Baki sidik dashi jikin Nan nata Kamar ka taba jini fito. Lekowa tayi tana musu sannu da zuwa tare da gaishe su tana fadar "ku shigo daga ciki Bari na Kira Ammar". Ta fada tana zura silifar a kafarta. Daya daga cikin su ukun ne ta tabe Baki ta kauda Kai tana fadar "kirawo ta tazo ba sai mun shiga ba tunda ba Zama mukazo ba" Ita dai Zahra gaba tayi yayin da su Zilai masu aiki suka zuba musu idanu suna kallon kallo ya junansu Dan daga Jin lafazinsu sun San ba abin Arziki ne ya kawosu ba. Kafin Ammah ta fito daga bangaren Abba sahura Daya Mai aikinta ta leka ta fadawa Mama anyi baki. Da ita da Asaben suka fito Asaben na fadin "lale barhabin kushigo Mana kun tsaya daga wajen" Wata ce daga cikinsu Bata farkon da tayi maganar ba tace "A"a Hajiya ba Zama mukazo ba munzo ne mu karbi kayan lefen da muka kawo na Sahal yace baya yi akai kasuwa". Lafazin da Ya yiwa Ammah sallama kenan lokacin data fito Zahra na biye da ita. "Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un" Abinda Ammah ta fada kenan a zuciyar ta Nan da Nan wani jibi ya taso Mata. Salatin Mama da Asabe ne ya fito da Alhajin daga part dinsa yayin da su Zilai sukayi cirko-cirko duk wuta ta dauke musu Dan maganar tasu ba karamin razani tasa a zukatansu ba. A hankali ya karaso kusa da Ammah Yana tambayar meke faruwa ne kafin tayi magana Mama tayi tsagal tana fadin "wane irin cin mutunci ne Alhaji ba laifi tsaye bana zaune zasuzo suce a Basu lefensu Wai auren amfasa". Ta karasa fada tana fashewa da kuka tana maganganu, ita kuwa Ammah ba abinda take sai ambaton Allah yayin da Zahra ta nemi gefen inda aka shuka filawoyi ya zauna Dan ji tayi Nan da Nan jiri Yana nema kayar da ita, itama bakinta ba abinda yake sai ambaton Allah. Kallo Daya Alhaji Jafar yayiwa Baki ya kawar da kansa Dan da alama da rashin mutunci suka shigo gidan. Gyaran murya yayi kafin yace "Masha Allah munji sakonku Amma Dan Allah ku koma kuce musu zuwa anjima inshallah Allahu za'a dawo da duk wani Abu daya kasance nasu ne har sadakin da suka kawo Allah yasa hakan yafi Alkhairi". Yana Gama fadar haka ya juya dakinsa ya barsu a Nan a teaye, Dan dukkansu ba karamin kwarjini yayi musu ba. Ammah part dinta ta nufa duk kwakwar mutum baze taba Gane Yanayin da take ciki ba.Dan Allah yayi Mata wata irin zuciya Mai iya danne bacin Rai da wuya ka Gane fushinta tana da hadiye fushi sosai, dakin suka bita suna Bata magana Mama sai sharbe take tana Dan Allah wannan wane irin cin zarafi ne da tazarce ace saida komai ya kankama sannan za'a bullo da wannan cin zatafin dan a wulakanta yarinya har a ringa yi Mata wani gani -gani aga Kamar wani Abu tayi yasa aka fasa". Sai lokacin Ammah tayi magana tana fadin "ba komai Mama Daman can haka Allah ya nufa ba mijinta bane Kuma maganar mutane su ringa ganin Kamar wani Abu marar kyau ne yasa aka fasa na barsu da Allah yayi Mani maganin komai, ba komai haka Allah ya nufa rubutaccen Al'amarine baya goguwa". Tana Gama fadar haka ta wuce bedroom dinta sun jima a falon suna tattaunawa kafin su koma dakin mamar su Zilai kuma suka nufi in da Zahra tace zaune suka dinga Bata magana duk da Bata want rude ba a nitsenta take. Duk wannan kwamacalar da akayi su Hameeda da Salma basa Nan sunje Aiken Mama. Tunda Alhaji Jafar ya koma daki ya kasa zaune ya kasa tsaye Bai taba zaton karamar magana daga gida irin Honorable ba Amma ya hanasu kayan ne Dan ya tabbatar da daga Ina maganar take shin da sanin uban yaron da waliyayansa ko Babu Dan yanda sukayi komai cikin girma da mutunci ya kamata ko baza'ayi auren ba to a rabu cikin mutunta juna. Su malam Bukar da Yayan Alhajin Wanda suke 'yan maza Alhajin ya Samu da maganar basuyi kasa a Gwiwa ba zuka nufi gurin waliyyan Sahal sai dai maganar haka take Dan sun tsame ma hannunsu daga lamarin tunda iyayensa Basu da lissafi, Wai yaron ne yace musu shi baze iya auren Zahrar ba yanzu ba wadda ya tsana kamarta duk duniya". Lokacin da suka dawowa da Alhajin wannan labarin ransa yayi matukar baci, a ranar aka maida duk wani Abu da yake mallakinsu ne. Sai dare Abban ya Samu kebewa da Ammah in da ya ringa tausarta da kalamai masu Dadi har ta Samu ta Samu nutsuwa Amma fa kasa kwana tayi a dakin nasa. Lokacin data dawo daki Zahra Bata tafi nasu bangaren ba tana dakin Amma a kan gadon tayi rigingine idanuta a rife hawaye na zurarowa daga gefen idon wani Abu yake Mata yukuki a zuciyar ta. Har Ammah ta bude kofa zahra Bata sani ba saida ta zauna a kiss da ita taji shashhshekar kukanta kasa -kasa. "Tashi zaune magana zamuyi". Daga sama taji maganar Sam bata San Ammar ta shigo ba. Ba musu ta tashi zaunen tana koge fuskarta da tayi wajir. "Meye dalilin da Sahal ya fasa Aurenki ko ya sanki 'ya mace ne". Cikin tashin hankali marar misaltuwa Zahra ta dago ta kalli Ammah kafin ta fasa kukan da take dannewa tana na zuci. Kai ta shiga girgizawa tana wani irin numfashi nKamar wadda zata shide. Kafin Allah ya batan ikon bude bakinta ta magantu. "Wallahi Ammah ban taba abinda kike tuhumata ba Koda wasa wallahi zan rantse Miki da Alur'an a bani zanyi Alwala in ratse, idan na taba Zina Ammah Allah ya haramtamin shiga Aljannarsa ranar Alkiyama" Ta fada tana wani irin kuka Mai taba zuciyar Mai sauraro. "Shitttt.....kada na Kara Jin wata magana makaranciyar wannan daga bakin ki. Ba zarginki nakeyi ba na kasa samun nutusawa ne tun lokacin da sabbin halayensa suka Fara fitowa, nake cikin zulumi da taraddadi saboda sanin yanda rayuwa ta Zama abinda ta zama, ba komai kansa yayiwa ke kuma Allah yayi Miki Albarka ya bakin Wanda yafi Sahal". Bata iya amsawa a fill ba sai a zuciyar ta. Tun bayan faruwar lamarin Zahra ke cikin damuwa Dan ma Haneeda tana tausarta da kalamai na kwantar da hankali. Ammah ta Kira su Ummee ta fada musu komai sun so kwarai zahrar taje Amma Alhaji Jafar yayi uwa yayi makarb'iya akan suzuzo idan hankali ya kwanta, da haka suka bar zancen. A Dan tsakanain ne Aunty Hasana tazo, sun Sha jajantawa sosai da Ammah itama sai da ta tsare zahra da tambayoyi kala kala, daga karshe ta Kare da nasiha Mai tsoratarwa sosai. Lokacin da zata koma Jos ta nemi zata tafi da Zahra Abban bai Hana ba Yana ganin idan tayi nisa da garin zatafi Samun kwanciyar hankali. Zamanta a Jos Mai Dadi ne Dan daga baya ma fafutukar nemar Mata admission mijin Aunty Hasanar ya Fara ba'a samu wadda ake so ba, sai diploma ya nemar Mata a wata private school ta Fara computer science. Hankalinta ya kwanta sosai ta cire soyayya daga zuciyar ta Sam taqi ba kowa fuska akan soyayya duk da yanda ake kawo Mata Rida. Ranar wata litinin sun Gama lectures dinsu na safe suna zaune da wata course mate dinta 'yar kabilar Tiv suna wani Assignment jininsu ya hadu da jannifer sosai Dan har gidan Aunty Hasana tana zuwa idan zasuyi wani aikin. Bayan sun Gama ne suka nufe caf'e na cikin makarantar a cire musu hard copy din aikin suka tarar da cinkoson mutane dole tasa suka fito waje ayi musu. Har sun Gama sun fito suna niyyar tsallaka titi ne wata mota Mai azabar kyau ta tsaya dai dai inda suke tsaye. A hankali na ciki ya sauke tinted glass din motar, wani guy ne da gani hutu ya ratsa shi sosai, murmushi yayi musu idonsa na kan zahra Yana fadin "sannunki" Jannifer ce to amsa masa Dan tana Jin hausa Kamar jakar kano. "Yauwa sannunka" ta fada. Kofar ya bude ya fito Yana sanye da kananun Kaya,fari tas dashi kamar irin ruwa biyu din Nan half cast Dan sumarsa a nannade take kamar irin ta buzaye din Nan. Cikin kwarewa da yadda da Kai kalli jannifer Yana fadar "Naga kawarki ne inso da fatan zakiyi min campaign". Dariya tayi tana kallon Zahra wadda tayi kicin kicin da fuska Kamar zatace wayyo Allah. "Gaskiya na tafi tunda Baki da aikin Yi ke saiki zauna". Zahra ta fada tana nufar titi ganin an Sami space din tsallawa. Jannifer da Dan jima dashi kafin ta shigo cikin makarantar, Koda ta shigo Bata yi Mata maganar komai ba har suka Gama lacture dinsu suka tashi. Direban su Aunty Hasana ya dauke su ya ajiye jannifer a hanya kasancewar su zahra sun gaba dasu Amma hanyarsu daya sau da Daman sukan tafi tare ranar da jannifer Bata zuwa shagonsu. Ranar Saturday misalin hudu da rabi haka su zahra da yaran Aunty suna compound din gidan tana Dora Yara kan lilo marry go round suna Wasa kusan duk weekend a Nan suke hutawa da yamma tunda islamiyyar safe suke zuwa a weekend. Mai gadi ne ya nufo gurin da suke Yana fadin Zahara'u ki fadawa yallabai Yana da bako a waje". Auntyn ta fadawa Abban su Faruq Yana da bako inji Mai gadi. Lokacin daya fito yayi mamakin da baiga bakon ba ya nufi gate Yana tambayar Mai gadi, shine yace "ni ne na hana ya shigo tunda yace bakasan da zuwansa ba bilhasal ma yace baka sanshi ba" Kofar Mai gadin ya bude masa ya nufi gurin da motar take yayin da shi kuma na cikin ya fito. Da gaske baisan yaron ba, hannu ya bashi sukayi musahiha sai Kuma sukayi shiru Ya Aliyun ne mijin Aunty Hasanar yace Masa "ko kaine maisallama Dani?". "Eh nine"sai Kuma ya danyi shiru. Ya Aliyun ne yace "my friend pls talk feel free with me". Nan yayi Masa bayanin yaga Zahra ne Yana sonta shine ya biyota gida, ya fada masa sunansa MUNEEB mahaifansa Kuma Alhaji Salman Mai fata. Kallonsa ya Aliyu ya karayi yayi mamakin yanda d'a Kamar na Alhaji Salman Mai fata yake da irin wannan tarbiyya ganin yanda mahaifansa yake da mahaukanta kudi Kuma yasan 'ya'yansa sosai Amma da yawansu gata yasa sun lalace basa ganin kan mutane da gashi. Ya Aliyun yaji dadi sosai ya Kuma bashi damar zuwa gurin Zahrar sannan ya Dan fada Masa wacece Zahrar a gurinsa. Lokacin da ya Aliyun ya koma bayani ya yiwa Aunty Hasana na abinda ya faru itama ta bada goyon baya tasan ko yanzu Zahra tayi gaba Allah ya Bata Wanda yafi Sahal Dan ba karya ba hadi a tafiyar. Da dare Aunty ta Samu zahra da maganar da farko tuburewa tayi akan ita Bata so saida Aunty ta fito Mata ta bayan gida sannan ta fashimci abinda Auntyn take son ta Gane. Washe gari Aunty har da ita aka hadawa MUNEEB abin tarba, Zahra ta Dade tana mamakin yanda akayi yasan gidan su Amma data Zama very curious sai ta gano duk yanda akayi jannifer ce ta bashi address dinta. Yau ma da yamma yazo, falon Ya Aliyu aka bude Masa yayin da Mai aikin Aunty shema'u ta Kai Masa abin tarba. Wata straight gown ta saka ta atamfa glitter Mai ruwan peach colour sai madaidaici gyale kalar lemon green irin touching din jikin atamfar sai takalmi shima lemon green din plat Mai kyau. Bata daura dankwalin kayan ba. Ta fesa turenta Amber oud gold, tun kafin ta karaso kamshin ta ya fada Masa zuwanta, kofar ya zubawa idanu ai lokacin data shigo da sallama Saida ya Dan samu shock na wucin gadi Ashe ranar ba inishin Zahrar ya gani ba yanzu ne yaga zahirinta, a kasa ta zauna kan carpet tana gaishe shi kanta Yana kallon kasa. Nan ya gabatar Mata da kansa da abinda ya kawo na son aurenta, bai matsa Mata na lallai sai yaji ra'ayinta a sannan ba shima bai jima ba ya tafi, bayan ta shigo ne Mai gadi yayi knocking a kofar falon shema'u ta bude manyan ledoji ne ya Mika Mata guda biyu yace a bawa Zahara'u inji bakonta. Tun daga lokacin Koda yaushe Muneeb yana hanyar gurin Zahra,r tun tana dari dari dashi har ta sake, shi mutum ne Mai saurin shiga Rai Yana da wasu Qualities da zasusa asoshi. Kafin su rufe wata biyu sunyi wata irin shakuwa ta ban mamaki duk Wanda ya kwana ya tashi a family din Mubeen yasan da zaman Zahra haka itama nata sun San Muneeb Dan har Azare yaje ya gaishe su da ashirin bama sha tarabta Arziki ba,har Saida Abban su yayi Masa fada sosai akan kada ya Kara musu haka in dai Yana son su Shirya. Sun daf da Gama diploma dinsu Iyayen Muneeb sukayi maganar aure, ba Bata lokaci aka saka Rana ba'a wani ja lokaci ba Mai tsawo ba, abu kama-kama shima Kamar na baya abun ya shashence ba wani cikakken dalili haka Nan Rana tsaka Muneeb yace ya fasa akayi juyin duniyar Nan yace shifa aure ba dai da Zahra ba komai za'ayi, dole aka hakura Dan shi cewa yayi har kayan ya bar Mata saidai abinda iyayenta Basu amince ba kenan. Fadin halin da zahra da su Ammah suka shiga bazai misaltu ba, Dan hankalinsu yanzu yafi tashi fiye da wancan lokacin. Ammah taso kwarai zahrar ta koma Azare Amman Maman Ya Aliyu ta roki Alfarmar zata Kai zahra gurin masu Islamic chemist a gani ko namijin Aljani ne ya aureta. Ammah ba tayi musu ba sai godiya tayi sosai, sunje harda Aunty Hasana anyiwa Zahra tambayoyi ba alamar Aljani a jikinta sai dai sun fada musu da alamar sihiri a tare da ita Amma ba sosai ba, Nan suka bada magunguna Hajiyar ta biya suka dawo gida. Jannifer ma tayi bakin cikin abinda ya faru taso Zahra ta Bata dama taje garinsu ayi mata wani Abu akan idan ma wani ne yake lalata lamarin auren zega abinda ze same shi. Nunawa tayi Bata so ita haka Allah ya tsara Mata wannan qaddarorin Kuma ba makawa sai sun sameta. A haka har suka Gama diploma dinsu kafin Aunty Hasana ta mayar da Zahra Azare. Haha rayuwa taci gaba da gudana, duk wani buri akan aure Zahra ta cire shi Bata kula kowa duk iya nacin mutum Bai isheta kallo ba, wani lokacin har fada suke da Hameeda akan rashin kula samari sai dai sau da yawa tana Mata uzuri akan irin yanda fasuwar aure take walagigi da ita. Zama ya Mika lokacin har anyi wurin wata Tara da fasa aurenta da Muneeb. Wani yammaci suna zaune a bayan part din Ammah ita da Hameeda da Mujiba data shigo musu yawan yamma suna hira Kiran ya Abdul Hakeem ya shigo wayar Hameeda Yana tambayar suna ina ne ya shigo Bai gansu ba. Inda suke ta fada Masa suna niyyar tashi ya zagayo bayan, a tare suka gaishe dashi ya amsa Yana gaisuwar tasu yana fadin "Congratulations" "For what Yaya?" cewar Zahra. Irin Brown din envelope din Nan babba ya Mika Mata Admissions letters ne guda biyu a ciki na Salma da Hameeda duk sun Sami gurbin karata a federal University Dutse jigawa state (F.U.D). Cikin murna ta rungume Hameeda tana fadin "congratulations sister". Kafin ta sake ta tana Mika Mata takardun, ai tana arba da wannan abin Arziki ta Diba a guje tana fadin"thank you Yaya Allah ya saka maka da Alkhairi". Bayan ta wuce ne zahra ma ta Kara Masa godiya sosai. Kujerar da Hameeda ta tashi ya janyo ya zauna alamun dake nuna magana Mai mahimmanci zeyi da ita. Ganin haka yasa Mujiba tashi tana fadin "Yaya sai anjima". "Dawo ki zauna ba Zama zanyi ba.magana zan fada Mata kawai" A takure ta koma ta zauna. Kan Zahra ya maida kallonsa "kina jina?" Kai ta gyada Masa alamar eh. "Good" ya fada. "Ina ga Nan da one month ko three weeks kema Zaki wuce Zuwa Turkey daga can Kuma idan komai ya daidaita Zaki wuce syprus inda Zaki hada a degree dinki, idan kin tuna Kamar two months da suka wuce ai na karbi komai naki to Mama Hanifa ce ta bukata a tura Mata a she makarantar zata nemar Miki taso a Samu a Nan turkey din to ba'a samu ba, ita kuma Bata son a Kara Bata lokaci, shine ta yiwa danta magana tunda a can yake aiki da ofishin jakadancin turkiyya na kasar Kuma ma Nan ne kawai Mama Hanifar ke ganin yafi kusa da istanbul din". Ba Zahra kawai ba hatta Mujiba tayi murna kwarai da gaske gatan da za'a yiwa Zahra kenan a irin wannan lokacin na a rabata da kasar gaba daya Kota Samu peace of mind. Godiya ta ringa yiwa ya Abdul Hakeem din harda 'yan hawayenta na Dadi. Gashi Ammah Bata Nan taje Jimeta gurin biki, taso tana Nan ta kwanta a jikinta suyi sharing din farin cikin. Har ya Abdul Hakeem din ya kai kwanar da ze fita ya juyo Yana fadin "don't talk to anyone, keep silent pls, nasan Mujiba Bata da problem shi yasa na fada a gabanta". Yasa Kai ya wuce. Kallon junan su sukayi suna son banbance maganar Ya Abdul Hakeem. 💋❤️ AUREN HUCE HAUSHI 💋❤️ MAMAN FATIMAH PAGE TWELVE (12) __________A cikin qanqanin lokaci aka Gama yiwa su Hameeda shirye - shiryen tafiya makaranta Dan sau biyu suna Zuwa jigawar akan registration din. Sai wannan ciccira kai salma keyi tana sakin maganganu bare idan suna dakinsu su kadai ta dinga fadin magana kenan, ko ci kanki zahra Bata ce Mata sai ma wani lokacin Hameeda ke kwabawa Nan da Nan Kuma su hau sama da ita. Ranar da zasu tafi harda ZAHRA a 'yan rakiyar, Mama ma taso zuwa Abba ne ya hanata ya Kama fadan me zatayo. Har hostel Zahra ta rakasu Lokacin da zasu taho ne Hameeda ta Fara share hawaye itama zahra ta Kama, Saida ya Hamza yayi musu Jan Ido suka daina kukan, Yayin da Ya Abdul Hakeem yake musu dariya Yana fadar "Banda tsabar shagwaba ta lalacewa har wani kuka kuke Kamar wasu 'yan J's one". Wani kallo ya ai kawa zahra na Baki Fara kuka ba.sai kin ganki a tsakiyar masu jajayen kunne tukunna Dan ma dai kema samman kalne ya gada a zuciyar sa. Sai bayan magariba suka dawo gidan. Ba'a fi sati biyu da tafiyar su Hameeda ba visa din su Zahra ta fito ita da Abdul Hakeem. Sai ana ya gobe zasu tafi Ammah ta fadawa Mama. Ai Kuma tayi korafin abin Dan har Alhajn ta fadawa yace shima jiya yake Jin labarin tunda Saida komai ya kankama sannan suka Kira suka fada Masa Dan kada ya Hana. Da safe Bala dureba ta dauke sai kano inda zasu tashi. Satin Abdul Hakeem hudu a can Dan Bai taho ba Saida ya raka Zahra har syprus din a gabansa komai ya kammala ranar da ze tafi Zahra tayi kuka Kamar idonta ze fita sai a sannan taga ba karamar wauta tayi ba data yarda da wannan karatun, dadin ta daya da uncle Haisam a kasar ko banza tana da gurin zuwa a debe Mata kewar gida. Ta Fara karatu cikin nasara Bata da wata matsala ta zahiri saidai sau da yawa tana shiga dogon tunani akan al'amuranta ta rasa Gane daga Ina ne ake samun irin wannan akasin? matsalar dai iri daya ce, Kuma salon tafiyar iri daya ce sai Dan banbancin da baza'a rasa ba. Suna yawan waya dasu Ammah da mutanen Jordan, lokacin data Kira Hameeda mita ta ringa yi Mata akan tana boye Mata wani Abu tunda gashi Saida ta bar kasar kana ta Kira ta. Da kyar ta fashimtar da ita abun ne yazo da gaggawa itama Bata sani ba Saida komai ya Zama ready, Kuma tayi ta try din ta sameta Bata Samu ba lokacin ana fama da matsalar network a area dinsu. Zahra najin dadin Zama a kasar duk karshen sati a gidan uncle Haisam take yin weekend din ta, sai Monday da safe motar Embassy take dawo da ita. Tsakanin syprus science University din wadda take kyrenia city a arewacin syrups din da capital city din dake Nicosia tafiyar kilometers talatin ne, kawai daga Baya ma da uncle din cewa yayi ta baro cikin makarantar ta dawo gidansa kawai da Zama sai a ringa kaita kullum itace taqi tana ganin Kamar abun da wahala yau da gobe sai Allah daga nesa nesa dai. Yau ma Monday da wuri motar Embassy din ta kawo ta, tayi gaba da wasu daliban zuwa mabanbantan makarantu inda suke karatunsu.Ganin da saura Kamar awa aya da rabi kafin su shiga lectures yasa ta wuce hostel Dan ta aje kayan da tazo dasu. Tana cikin tafiya tazo gota wani hostel Kamar a mafarki sai taji Kamar ana hausa a dakin abin ya Bata mamaki tayi Kamar ta koma ta duba sai dai tayi gaba tunda bin kwakwkwafi haramun ne. Lokacin da suka Gama lectures din Bata koma hostel ba, karatu suka zauna sunayi da wata course mate dinta 'yar kasar Lebanon Asseyeh tasu tazo daya sosai saboda itama akwai nacin karatu ga Kuma kwanyar Allah ya hore itama, uwa uba ga rikon addini tunda su dai kasar sai a hankali kawai culture din ta rinjayi addinin, Dan wasu Ma sai kaga suna sallah zaka Gane musulmi ne. Yamma likis su Zahra suka nufi hostel, haka nan Zahra taji tana son karabi ta wurin inda taji ana magana da Hausar nan, can ta nufa bayan sun rabu da Aseeyeh. Very lockly kuwa tayi Dace da wata daga ciki ta fito tana waya bahaushiya sosai.A shape ce a jikinta ta atamfa sai karamin hijabi a jikinta da alama Kamar fita zatayi.Dan tsayawa zahra tayi har ta karasa wayar, cikin nuna zallar farin ciki zahra ta nufeta tayi Mata sallama. Da sauri ta juyo Jin an Mata magana da Hausa cikakkiya. "Wa'alaiki Salam" yarinyar ta amsa Mata tana kallon zahrar da murmushi itama a fuskarta. "Masha Allah wallahi naji dadin ganinki kema daga Nigeria kike". Zahra ta tambaye ta. "Eh daga Nigeria muke muna da Dan yawa zamu Kai goma". Mamaki ne ya Kama zahra ganin Bata taba ganinsu ba Koda wasa. "Ikon Allah! Amman dai baku Dade ba ko?" Kai ta gyada "Mata gaskiya Kam ai ba school daya muke ba mu a Nan mu hudu ne, sauran suna different Universities ne on transfer mukazo nan daga Sudan tunda can rikici ya d'ai d'aita Qasar. Zo mu shiga ciki ki gaisa da sisters Dina kafin na dawo zan fita na samo Ko fizza ne yau bamuyi girki ba". Ta fada tana juyawa ciki, bayan ta zahra tabi suka nufi ciki. "Khadijah ! Fatima,! Sajida! Kuna Ina ku fito gashi mun Samu qaruwa". Kowacce barin abinda take tayi ta nufo kofar tana fadin "Anisa menene?". Ai kafin tayi magana Zahra tayi Arba da sajida Musa, sajidar ta ta FGGC KAZAURE. Cikin wani irin farin ciki suka rungume juna Zahra sai kuka Dan wani abune da Bata taba zata ba robonta da sajidar tun suna cikin bala'in Sudan kafin wayar sajidar ta salwanta shi kenan suka daina Jin juma Amma kullum zahra da fargaba take kwana har zuwa lokacin da ta Samu labarin dawowar su sajidar a bakin Maryam Suraj wata kawarsu. Kallo saiya koma sama Wai shaho ya dauki giwa ita Mai kawo bakuwa sai duk suka Zama 'yan kallo. Hannun zahra sajidar ta Kama ta nufi bed in ta da ita tana fadin "wannan wace irin ranar farin ciki ce bestie wallahi ranar nan tana daga cikin ranekun da bazan taba mantawa dasu ba cikin tarishin zamana a syprus, pls bestie talk ya akayi haka ta faru Dan Allah kece ko gizo idona yake mini ne Dan Allah kiyi magana". Ita dai zahra ba baka sai kunne, ai ita nata mamakin yafi na sajidar sau dari idan da Wanda Allah ya yiwa gyadar dogo ai ita ce, ba zato ba tsammani Allah yayi Mata irin wannan suturar bama 'yan Nigeria ba A'a aminiyar ta sukutun ya kawo Mata kasar, ba abinda zata cewa mahalicci sai godiya take a Nan tayin sujudushshukur ga Allah. Sai da ta goge hawayenta sannan ta Samu damar magana suka gaisa da sauran yayin da Anisar ta cire hijabin tana fadin "Ai Kuma saidai kowa ya hakura da cin fizzar Dan na fasa fitar kawai ayi abinci tunda Naga bakuwar tamu ce ko sister" ta fada tana kallon sajida. "Kwarai kuwa ai dukkanku kowa ya kwana da sanin Zahra Muhammad sani ko?". Gaba daya suka zubawa Zahra idanu suna fadin sosai ma kuwa, niba har gaisawa munayi ba some times idan Kuna vedio call lokacin muna Sudan" inji Khadijah. "To ai ita ce gata a gabanki zahiri" Khadijah ta Dade tana mamakin abun ita sai taga Kamar canza Zahra akayi tasan dai yesss ba karya zahra Mai kyauce na a bugi kirji a fada, amma sai taga wannan Kamar ma Bata taba hada dangantaka da 9ja tamu ba, komai nata classic ne. Nan suka baje hajar hirar yaushe gamo, har kusan karfe goma na agogon kasar suna tare anan su sajida suka fada Mata gwamnatin tarayya ce ta dawo dasu Nan tunda suna under scholarship ne shine aka rarrabasu kasa kasa su Allah yasa suka shigo cikin daliban da aka kawo Nan din. Har daki suka raka Zahra a Nan ta Basu fizzar tunda Daman tazo da ita daga gidan uncle Nan ma sun jima kafin su koma. Ai tun daga ranar wata nutsuwa da kwanciyar hankali suka Samu kyakykyawan muhalli a zuciyar Zahra, haka itama sajidar duk da Daman ita tana da masu dauke Mata kewar gida, Suma su sajidar sau da yawa suna bin Zahra a wasu weekend din zuwa gidan uncle Haisam din Amma su basa kwana duk da irin nacin da zahrar ke musu. A haka karatunsu ya Mika har sukayi exams, Mama Hanifa taso Zahra taje Mata tayi hutu Amma Haisam yace tayi hakuri sai hutun karshe session. A haka suka Kare hutunsu suka Dora da karatu, ba Sajida ba hatta su Khadijah suna Jin dadin Zama da zahra gashi Sam abin duniya Bai rufe Mata ido ba, Dan ta ko'ina kudi ne ke sauka a Account din ta ba daga 9ja din ba, ba daga Jordan ba, ba daga turkey ba, kowa kokarin farantawa zahra yake zuwa lokacin tayi wani irin mahaukacin kyau na ban mamaki ga wayewa da wayon zaman duniya ta Kara Zama 'yar gayu Kamar me Dan ba karya matar Uncle Haisam Yar gayu ce sosai kamar Auntyn ta Hasana tasan yanda ake tattalin jiki matuka. Har zuwa lokacin ba ruwan Zahra da saurayi bil hasal ko aboki namiji Bata dashi, akwai wani Dan Syria Omer yaso Zahra Kamar kaddara Amma ta shafawa idanunta toka tace ba wannan maganar yace to su Zama friends Nan ma tace lah lah. Dole ya hakura saindai duk inda zasu hadu sai yayi Mata magana idan abu ta saya duk yawan kudin shi ze biya. Lokacin hutun karshen shekara Zahra taso zuwa Nigeria tunda taga su sajida nata Shirin tafiya, ta kwallafa Rai sosai akan zuwan Amman sai Ammah ta hanata zuwan tace taje Jordan idan hutun ya kusa karewa ta dawo Nan gurin Mama Hanifa ta karasa Abdul Hakeem zezo ya ganta. Ba haka taso ba da har tayi niyyar Kiran Abban ta fada Masa sai Kuma tayi tunanin kada Ammah tace ta Kai Kara dole ta hakura tunda Bata San nufin Ammah din ba data hanata zuwan. Taji dadin zuwa Jordan din sosai, dan Ummee na Shirin zuwa Saudi Arabia ne ma zuwan Zahrar ne ya kawo Mata tsaiko, tare suka tafi bayan ta huta, a can suka tarar da Aunty Nawwara wadda taje zuwa na musamman tunda lokacin ana daf da bikin aurenta inda za'a kaita Bagdad (Iraq). Sunyi sati daya zuwa suka nufi makka sukayi Umara, sosai Zahra ta mayar da hankali gurin addu'a akan matsalolinta na yanda rayuwa ke walankekuwa da ita Bata rasa komai ba Amma aure Yana neman yafi karfinta dah kudi ko kyau ke sawa mace ta auru tasan da yanzu ba wannan zancen ake ba, sai dai tasan duk Dan Adam baya wuce tasa kaddarar sai dai neman sauki gurin Allah s.w.a. Madina suka koma da suka Gama umarar,basu Dade ba suka koma Jordan. Lokacin da hutunsu ya taho garewa zahra ta koma syprus. Gidan uncle ta Fara Zama kafin daliban su dawo tunda ana saura one week ayi resuming ta dawo. Karatu suke ka'in da na'in ba Kama hannun yaro, amincin ta da Sajida ya Kara karfi tamkar uwa daya uba daya suke, Dan lokacin da sukaje hutu sajidar har Azare taje ta gaishe da Ammah ta karbowa Zahra sako. Duk lokacin da za'a yaye dalibai makarantar tana hada gagarimin taro tana baiwa best student na kowane department award. A karshe semester din ne aka hada taron Wanda ya Tara al'umma daban daban daga kasashen duniya masu Taya 'ya'yan su da 'yan uwa murnar gama karatu, celebration ne ake na gasken gaske, su zahra dai suna kallon abubuwan tunda wannan shine na farko da akayi suna Nan lokacin da akazo bada award ne ba zato ba tsammani aka Kira zahra Muhammad sani daga Nigeria aka Bata award na overall a department dinsu akan kowane subject. Wayyo murna gurinsu ba'a magana Dan Zahra kuwa har mukan Dadi tayi data duba taga yawan daliban da suke a department din nasu Amma ace ita ta karbi best ai abin murna ne Kam. Sun Sha hotuna da mutanen mu na africa more especially 'yan Nigeria. A ranar Zahra tayi takaicin karatun nesa da ace a gida ne da Abbanta ko Ammah ko wani daga cikin yayinta zata danqawa kyautar su sharing happiness din tare Amma Nan kuwa fa sai da friends da wasu tsirarun mutane Wanda ma ba saninsu tayi ba sukayi farin cikin, ga Uncle Haisam ma a matarsa da yaran duka sun tafi turkey. Sai ta waya sukayi murnarsu da jama'ar gida ta tura musu hoton award din ta waya hotunan da suka dauka. ----------------- AZAREN KATAGUM Alhaji Jafar ne da Malam Bukar sai Habibu dan kanwar malam Bukar dake aure a suleja malam din yake rikonsa tun yana karami mahaifinsa ya rabu da mahaifiyar sa acan gida Yobe da tayi auren a suleja din ne baban Habibun yace baza'a tafi Masa da yaro gidan wani ba yayi agolanci, rigima sosai aka kwasa da shi saboda itama tace bazata bar danta a inda za'a kashe Mata shi ba. Shine mafarin malam din ya dauko shi tunda ba wasu 'ya'ya yake dasu da yawa ba, a hannun malam ya girma shi yayi karatun boko har matakin HND. Jikamshi malumfashj zasuje Daurin Auren 'yar abokin Alhaji Jafar din sannan zasu shiga Jikamshi dubiyar malamin malam Bukar din daya kwanta kwanakin baya a Asibitin Ibadan nisa yasa shi majiyyacin ya Hana masu zuwa dubiya sai yanzu daya dawo gida ne malam zeyi amfani da wannan damar yaje dubiyar. Tafiya ce mikakkiya Dan tsakanin Azare da malumfashi tafiya ce ba kadan ba Dan haka sukayi sakko Habibun ne ze tukasu malam Bala anyi Masa Rashi acen garinsu Itas gadau Yana can. Cikin ikon Allah Basu rasa Daurin auren ba Dan Sha buying Mai kyau suna cikin garin malumfashin. Basu Bata lokaci ba suka dauko hanya sun biya jikamshin sun duba malamin Alhaji yayi masa kyau ta girma. Suka dauki hanya sosai Alhaji Jafar ya yaba da tukin Habib Dan baiyi zaton ya kware irin haka ba. Sunzo kachako lokacin sallar la'asar yayi guri suka Sami inda akayi wani Dan masallaci dan matafiya. Suka firfito Dan gabatar da sallar, malam ne ya Fara gewayawa yayi dahara sannan Shima Alhajin yayo sukayi alwala suka shiga sallah Saida suka Gama suka fito sannan Habib Shima ya nufi gurin you daharar Amma shi saiya nufi wani bangaren daban, Bai jima da tafiya ba sai gashi da sauri Yana Kiran" Baba malam! Kuzo ku gani". Da sauri suka nufi inda yake harma da wani mutum da suka Sami a gurin Kamar Mai kula da gurin ne Dan daga gefe da 'yar tiredar shi suka rankaya Habib na gaba suna bin shi tun kafin su karasa suka hango mutum a kwance Kamar marar Rai. "Subhanallahi "abinda suka gada kenan suna karasawa kusa dashi sai da suka matsa sosai suka Gane da ransa Amma Yana cikin wani yanayi, dako dako sukayi aka rasa ya za'ayi dashi matashi ne ba zefi sana'an Habibun ba saidai a yanayin yanda jikinsa yake ba alamar wahala a tare dashi. Habib ne ya matsa kusa dashi sosai ya tsuguna Yana dudduba jikinsa ko akwai alamun duka ko makamancinsa amma babu komai, shawara sukayi su daukeshi kodan ceton Rai su tafi dashi idan yaso sai su dauki hotonsa a Dora a social media wata kila a Dace. Lokacin da suka shigo Azare ana sallar insha'i directly asibiti suka nufa dashi ma'aikatan nan da Nan suka duqufa a kansa, sai gurin Sha daya Allah ya taimaka ya kawa kwakwkwaran numfashi. Sai lokacin suka nufi gida malam ya turo dalibansa guda biyu ya fada musu dakin da aka kwantar da Wanda suka tsinta din, ya basu kudi saboda abun bukata. Haka su Abubakar suka kwana da shi sai gurin hudu da rabi na Asuba ya bude idanunsa Yana kallon bakon gurin da yake ciki ga bakin mutane a gurinsa, yukurawa yayi ze tashi yqji ya kasa kansa Kamar an Dora Masa dutse, bakinsa ya bude zeyi magana yaji kwata kwata ya kasa yayi yayi Amma Sam maganar taki yuwuwa sai hakuri yayi ya zuwa bawa sarautar Allah ido. ,💋❤️ 💋❤️ AUREN HUCE HAUSHIN 💋❤️ 💋❤️ ✨ MAMAN FATIMAH ✨ ✨PAGE THIRTEEN ✨(13) __________Washe gari daga gidan Alhaji Jafar Abdul Hakeem da magaji suka kawowa su Abubakar abinci Asibiti, sun tausaya bawan Allah nan sosai Dan zuwa lokacin sun fuskanci baya magana Kuma jikin ma baya motsuwa yanda ya kamata, toilet ma sai da sukayi Kama Kama suka kaishi, a haka su malam suka shigo Asibitin tare dasu Malam Mudi, Basu Dade da zuwa ba likitoci suka shigo round sun tambayi menene Asalin ciwon to su dai sun fada musu Yan suka hadu dashi Dan Basu da masaniyar komai akai. Gwaje -gwaje suka rubuta ayi Masa Dan binciken lafiyarsa. Basu Dade ba suka koma gida saboda a ranar Alhaji Jafar ze shiga Bauchi suna da meeting da gwamna Amma ya bar kudade a hannun Abubakar saboda magani da sauran hidimar Asibitin. Da yamma Habib ma ya shigo ya duba marar lafiyar nasu, Wanda har lokacin baya magana. Likitoci sunyi iya nasu binciken basuga komai ba a tare dashi, sai dai rashin maganar kawai Amma Kuma Yana Jin komai da ake fada. Bayan sun Gama bashi taimakon daya kamata suyi Masa suka sallame shi, Magaji ne ya dawo dasu gidan malam, Nan dakin malam na waje aka ajeshi tunda aka dawo dashi gida malam ya dukufa da Yi Masa addu'a Dan yayi bincike akan lamarin ya fashimci inda matsalar take, har Taraba ya tafi gurin malaminsa da yayi karatu a gurinsa ya fada Masa matsalar yaron, kwanansa biyu ya dawo Azare aka dukufa da rokon Allah da maganin hausa, haka zalika Alhaji Jafar ma Yana taho Masa dashi daga wani Islamic chemist da yayi musu bayanin matsalar yaron a can Abuja. Cikin ikon Allah ba'a rufe wata hudu ba ya Fara magana sai dai idan yayi sau daya sai a wuni bai sake wata ba. A haka aka dunga bashi taimakon har Allah yasa ya dawo normal Yana magana. A lokacin ne malam ya zauna dashi da Habib suka fada Masa inda suka same shi da halin da yake ciki a lokacin shiru yayi kafin yace musu shi dai yasan wata Rana Yana gida ciwon Kai ya takura masa har ya kasa fita, jzuwa dare yasha magani ya kwanta, to tun daga lokacin bazece ga yanda akayi ba shi dai ya farka ne ya ganshi a Asibiti tare dasu a hankali Kuma ya Gane a wani garin ma yake daban ba garinsu ba. Lokacin da Alhaji Jafar yazo garin malam ya fada Masa komai yanda sukayi da Mahmud din, Alhajin yasa aka Kira shi ya Kara jajanta Masa sannan ya nemi ya fadi garin nasu a mayar dashi Dan da gani Dan manyan mutanene. Nan fa ake yinta Dan kekashe kasa yayi yace shifa ya manta sunan garin nasu akayi juyin duniya yace sai dai ko Nan gaba idan Allah ya nufa ya tuna, abinda ya tuna ma daga baya tunanin yazo Masa, haka suka hakura badan sun amince ba bayan ya tafi sun tattauna da Malam din akan lamarin inda Suke hasashen ko bacin Raine ya baro shi da gidan ya gwwmmace yayi zaman sa a Nan kafin ya huce ya nemi komawa gidan. Nan yaci bada da Zama da Malam Yana kwasar ilimi kala kala. Nan da Nan ya Zama Dan gida suka dinke da Habib duk da ze iya girmar Habib din da Kamar shekara biyu dan yayi Kamar sa'an Abdul Hakeem. Bai cika wata shida ba Allah ya kawo aikin NGOs din Nan Wanda aka sakewa makarantar fasali da tsari suka sayi wani katon fili na makudan da sunan makarantar akayi gine ginen hostel din Yara suka dauki ma'aikata suka gyara tsarin karatun saboda kwazon Mahmud har co-ordinator din Shirin Muhammad Sameer ya dauke shi aika a shiyyar Katagum local government din ya Zama shine idon su a Nan, tunda ya iya rubutu da karatu. Habib ma Yana bada gudunmawa sosai a aikin duk da Shima nasa aikin da ma'aikatar ruwa ta Nan local government din tasu. Wannan kenan. ____ Syprus. Zuwa lokacin su zahra karatu ya Mika, tun tana saka Rai da zuwa Nigeria har ta hakura Kuma abinda ya Kara Bata mamaki sau biyu Abba da Abdul Hakeem suna zuwa ganinta idan harkar kasuwanci ya kawo sun Istanbul.Amma Koda wasa Basu taba ce Mata ga lokacin da zataje gida hutu ba. A haka har suka hada shekara biyu a kasar, da gaske gida take son zuwa shi yasa lokacin da hutunsu ya gabato batayi shawara da kowa ba ta kama shirin barin qasar, online tayi komai Kamar su Sajida sai da komai ya Zama daidai sannan ta fadawa Uncle Haisam Shima bai hanata ba yasan tayi hakuri, Mama Hanifa ma ta waya ta fada Mata Nigeria zata wuce kawai, haka Ummee ma ta wayar itama ta fada Mata taso ta hanata Amma sai tayi wani tunani kawai tayi shiru kudade dai to tura Mata masu yawa Wanda har saida Zahrar ta Kara kiranta tana tambayar kudin ma meye haka da yawa? Tace ta turo Mata ne kawai ko idan take zatayi wani abun, godiya tayi Mata sosai hakan Kuma dabi'ar Zahrar ne komai kankantar Abu idan akayi Mata alherinsa zatayi godiya Kuma ko waye ta Bata Bata duba ai iyayene. Kwana biyu suka Kara da akayi hutun shima visa din su Khadijah ne Bata Zama ready ba. Lokacin da jirginsu ya dauka a Aminu Kano international airport taji ta sauko ta shaqi iskar Nigeria ji taji Kamar a Aljanna take lallai kowa yabar gida gida ya bar shi, saukar safe sukayi wurin karfe Sha daya ba yanda su zahra da Khadijah Basu da zahra ba akan ta zauna ta Dan huta kona awa daya ne a gurin sajida Amma tace A'a Azare tayi Kira su Anisa ne da Fatima suka bi Sajida Su dan huta kafin driver dinsu ya karaso tunda ba nisa tsakanin kazaure da kano, Kuma Gwammaja kan hanya ne. Shatar taxi Zahra ta dauka ta kaita Kano line Dan direban taxi din ta tambaya Ina zata samu motar zuwa Azare ya fada Mata akwai gurare Amma ita Kano line yafi Mata kusa. Har cikin Tasha Mai taxi din ya shiga da ita gurin motocin arear Bauchi, tayi Masa godiya sosai ta kuma Kara Masa kudi akan yanda ya bukata. Away biyu da rabi Mai kyau matarsu zahra ta shiga Azare tun shigowa su ta Fara ganin 'yan canje canje a garin Kamar sabbin titina street light na solar sai gine gine masu kyau. Masha Allah ya dunga fada a zuciyar ta, Mai adai daita ta Sami ta fada Masa inda ze kaita, tunda suka tinkaro unguwar naji want irin nishadi ya mamaye ilahirin zuciyar ta, unguwar tasu ma an Sami cigqba sosai ga wasu gine gine sabbi masu kamar makarantar kwana har da gate a gurin gidan malam Baba gidansu ma gaba daya ya canza anyi Masa mahaukacin gyara tamkar sake sabo akayi. Lokacin da Mai adaidatan ya sauke ta dai dai lokacin ya Hamza ya fito da alama wani gurinzeje Nan kusa. Da madaukakin mamaki yake kallon zahrar shi dai Koda Wasa baiji ance zatazo ba Kuma yasan da ansan da zuwanta ai Bala driver ko su suje su daukota a kanon. Da sauri ya karasa Yana Mata sannu da hanya ita Kuma tana gaishe shi, shi ya biya Mai Dan sahun yace ta shiga ciki za'a shigo mata da kayan. Tunda ta shigo gate din tasan eh lallai gidan ya lashe makudan kudin Dan gaba daya an canza fasalin gidan, tunda ta shigo gidan Mai gadin ke kallon zahra Dan shi dai sabo ne Bai Dade ba ta dai gaishe shi tayi gaba Nan ma wani mamakin ya rufe shi Jin tayi hausa radau Dan shi dai ze iya rantsuwa da abinda ze kashe shi wannan ko zo Bata sani ba da Hausa. Ai mamakinta Bai karu ba Saida ta shiga cikin Nan dai ko rantsuwa tayi ba kaffara sabbin gine gine ne dam kwata kwata inda parts din su na da yake gurin ba komai sai filing da shuke shuken flowers. Lokacin data shigo gidan ba motsin kowa kamar ba mutane a gidan kowa ne kofar part Yana rufe Ido ta lumshe tana shakar iska Mai Dadi ta gidan. Idonta na nufen Nan tana tsaye Dan ita batasan wane dakin zata nufa ba tunda da gaske ta Zama bakuwa a gidan, maganar Ibrahim taji Mai bin magaji Yana fadar "kai!" Da karfi ya juya a guje Yana fadin Ammah! Ammah! Kizo ga Aunty Zahra a tsaye a kofar part din Mama". Magaji ne dake zaune a falon yana kallon wani series na 'yan Lebanon ya dago Kai da sauri daga kallon T.V Yana tsaki Yana fadin Amma Kai ba karamin soko bane dallah Banda tsabar hauka zaka wani ware murya Kama kwala Mata akan shashancin Kawai Wai zahra A'a wat......" Maganar ce ta makale Masa lokacin da zahrar ta kunno Kai ciki da sallama a bakinta, dan a bude yabar kofar saboda zumudin ya kawo labari. Ammah ce ta fito da sauri tana fadin Wai Kai har abada Ibrahim bazaka giirm..." Idonta ya sauka akan Zahra wadda tayi tsaye ta langabar da Kai tana kallonsu,kafin Ammah ta dawo daga duniyar mamaki sai Jin zahrar tayi ta rugumeta ta saki shashhshekar Kuka. "Ikon Allah!" "Ikon Allah!" Abinda bakin Ammah ke fada kenan, ita Kuma zahra ta riketa kamar zata bace Mata. Mamace ta shigo dakin da sauri tana fadin "Ina zahrar yanzu sahura ta shiga ta fada min taga Zahra ta shigo yanzu". Ta fada tana kokarin Zama idanunta suna kan Zahrar. "Wallahi kuwa Mama kin ganta Nan yanzu Ina daki Ibrahim ya shigo a guje Yana fadin gata Nan a waje nayi zaton shashancinsa ne Saida na fito na ganta kwatsam ba zato ba tsammani ba wani bayani". Ammar ta saki da Dago kanta tana goge hawayenta tana fadin. "Haba Ammah an kaini wata uwa duniya an manta Dani idan nace zanzo ace A'a ni Kuma wallahi na gaji gida nake so shi yasa naki fadawa kowa na tasho kawai na gaji da ganinku a waya ni zahiri nakeso". Ta fada tana maida kanta jikin kafadar Ammar. Tunda ta Fara magana Mama ta kureta da ido dan wani irin mahaukacin kyau taga Zahrar ta kara, ga wata irin gogewa da wayewa tamkar ba Zahrar data sani ba komai nata ya canza har ma salon yanda take magana. "Ai kodai ki daina irin wannan kasadar ta tahowa daga uwa duniya irin wannan ke kadai sai ki fada ko addu'a ayi Miki sannan aje a daukoki daga Kano, Amma fa Ina tunanin a motar haya kikazo garin Nan ko?" Mama ta fada. Kai Zahra ta gyada alamar eh, dai dai lokacin Yara suka shigo da jakunkuna ta guda biyu. zaunawa tayi tana gaishe dasu Ammah, sannan magaji yayi Mata sannu da hanya Yana fadin "irin wannan surprised haka uktiy? kin ganki kuwa kin juye Balarabiyar ki sak kodan kina cikin 'yan uwa dangi farare irinki" Dariya Zahra tayi Masa kawai. Ibrahim ne ya shigarwa da Zahra jakunkunan ta dayan bed room din Ammah, ya fito ya nufi kitchen ya kawo Mata ruwa da lemo, ya koma ya dauko warmmers din abinci sai Ina yaka saka yake da zahra har Mama na Masa Dan biki. Saida tayi wanka taci abinci sannan suka zauna da Ammah bayan sallar insha'i, hira sosai Suke Amma duk yawanci korafin Zahra ne na hanata zuwa.da Ammah tayi, a haka Abdul Hakeem ya samesu Shima yayi mamakin ganin.zahra kamar a mafarki Dan lokacin da ta dawo baya nan yaje Darazo ganin ganin wasu gonaki da Ya Hassan ya saya a can. Sun raba dare suna Hira da 'yan uwanta a falon Mama sunyi waya ma da Abban tunda lokacin Yana aAbuja, Shima yayi fada sosai lokacin da Ammah ta Kira shi ta fada Masa ga zahra tazo. Sai da ta kwana biyu tana huce gajiyarta, tana jikin Ammah kullum kamar kamar wata 'yar yaye, duk 'yan uwan kowa nan nan yake da ita, kowa kokarin kyautata Mata yake yi. Sunyi waya da Aunty Hasana tace Mata tana nan tafe Jos zatayi Mata sati Amma sai Abba ya dawo, haka kusan Kullum sai sunyi waya da Hameeda. Ranar data kwana biyar ne Ammah ta takura Mata akan ta leka makwabta ta gaishe wasu da yawansu sun shigo, wasu Kuma sun turo yaransu suyi Mata sannu da zuwa harda abin hassafinsu. A waya Zahra ta Kira mujiba akan ta Shirya ta rakata Nan gidajen su shishhiga a gaisa. Doguwar Riga ta saka kirar Dubai blue black Mai duwatsu tun daga sama har kasa ta saka plat she dinta fari tas ba wani makeup da tayi powder kawai ta saka sai lipsglow turarenta na Alkawari ta fesa Mai sanyi kamshi, Kota sa ko Bata Saba komai na sutarata kamshin yake. Ta fito Kamar wani dawisu Dan da gaske zahra mai kyauce komai nata Kamar ita ta zabarma kanta. Tunda ta shiga bedroom din Ammah ke kallonta data ita sai halicinta suka San abinda zuciyar ta ke ayyana Mata a fili Kuma sai tace "Masha Allah! Har kin shirya?" Kai ta gyada Mata tare da fadin "Eh Allah Dan dai kin matsabe Ammah Allah da Babu inda zani sai nayi sati biyu ko gate ba leka ba". Wata leda Ammah ta Miko Mata tasa hannu ta karba tana tambayar "na waye?" " Idan kunje gaida Baba malam saiki bashi tasa tsarabar turarika ne". Murmushi Zahra tayi har fararen hakoranta suka bayyana tana fadar "wace irin tsaraba Kuma Ammah nida ba Hajji naje ko Umara ba daga makaranta fa na dawo hutu". "To Miko min kije hannu sake ki gaisa ki taso tunda Zama da turawa ze saka ki koyi rowa" ta Mika Mata hannu alamum ta Bata ledar. Dariya tayi Zahrar tana fadin "Allah ya Baki hakuri Ammah Ina ni Ina koyo rowa a garin wasu alhalin na gaji kyauta gaba da baya Allah qara lfy". Ta nufi kofa tana fadin "saina dawo" "Allah ya tsare Kya gaishe da Malam din. Gidan su mujibar Zahra ta Fara shiga suka gaisa da Mamanta sannan suka shishhiga gidajen suka gaisa, gidan Malam ne na karshe, a hanya Zahra ke tambayar Mujiba ginin da taga anyiwa Almajiran Baba Malam? nan ta fada Mata iya abinda ta sani akai. A cikin rumfar canopy din da Malam yake bada karatu Zahra suka tarar da Malam din suna magana da wani matashi sukayi sallama a bakin rumfar a tare malam da Wanda Suke magana suka amsa sallamar, Yana fadin Bari naje na karbo yanzu in Sha Allah. Juyowar da zeyi sukayi ido hudu da Zahra wallahi ita dai batasan lokacin data rufe idanunta ba Dan wallahi wani Abu ta gani a idonsa Wanda Bata taba gani a idon kowa ba take zuciyarta ta wani harba a cikin girjinta. Ga wani mayen kamshi daya cika Mata hanci ita dai Bata San ya wuce ba Saida Mujiba ta tabata tana fadin ki bude idonki "Zahra menene?". Ajiyar zuciya tayi a hankali tace "ba komai muje" Cikin rumfar suka shiga suka zauna daga gefe suna gaida malam din. Amsawa yayi Yana fadin Masha Allah da bakin turai ne Fatimah yaushe Kika shigo ban sani ba kodon Alhaji Yana Abuje shi yasa bani da labari". Sunkuyar da Kai zahra tayi tana fadin. "Ban Dade ba Baba Malam yau kwanana biyar da dawowa, Saida na huta nace Bari nazo na gaisheka" "To Masha Allah! Allah yayi Albarka ya bada sa'ar abinda akaje nema, ai ba'a Gama karatun ba ko?". "Eh da sauran shekara daya karatun ne da banbanci da namu na nan tunda su basa yajin aiki". "Wannan haka yake, Allah yayi jagora ya bada sa'a" "Amin" suka amsa tashi zahrar tayi ta karasa gaban malam din ta aje Masa ledar turarikan dake hannunta tana fadin "gashi Baba ba yawa" Godiya yayi sosai kafin yace "ku shiga ku gaisa da zainabu batajin Dadi tana fama da masassara tun jiya". "Allah ya sauwake"suka fada suna fita faga cikin rumfar. Tunda suka shigo gidan suka sallama Amman gidan shiru a falon ma ba kowa uwar dakin Zahrar ta nufa tunda gidan ba bakonta bane, can tsakiyar gado ta hango Iya Abun jikinta yana ta kadawa tana ta rawar sanyi da sauri Zahra ta karasa kusa da ita tana Mata sannu Amman Sam ta kasa amsawa hannunta Zahrar ta Mika ta taba jikinta sai taji Kamar wuta. "Ya Salam". Ta fada tana nufar falon inda tabar mujiba tana fadar "Bari na fadawa Baba Malam jikin Kamar ya matsa gaskiya". Tayi waje ba tare data jira taji abinda mujibar zatace ba. Tafiya take cikin sauri burinta ta Isa gurin malam ta fada Masa abinda kenan. Ita dai Batasan yanda akayi ba sai ji tayi ta bugi kirjin mutum da kanta abinda yayi sanadiyyar ta tafi taga -taga zata Fadi taji an fusgota da Dan qarfi kafin ta Kai kasa sai ganin ta tayi rungume kane kane a jikin koma wannene an saka hannu biyu an zagaye bayanta. Kici kicin kwace jikinta ta shiga yi data Samu ta Sami kanta coming fishing ta daga ido taga wane Mai tarar aradu da fadin Kaine ya kwakumeta haka da yammcin Allah wata'ala ta sauke Masa zallar rashin mutunci duk da ba halinta bane, tana daga Kai sukayi arba dashi ya kafeta da idanunsa masu wani irin kaifi da mugun kwarjini a cikin nata idanuwan Wanda a ganinta dashi na farko ya yamutsa duniyar ta .AUREN HUCE HAUSHI MAMAN FATIMAH Page Fourteen 14. -----------kusa da ita ya matso sosai Kamar ze Kara rungumo ta, da sauri tayi baya tare da rufe idanunta ruf zuciyarta na Kara speed, a hankali yayi magana saitin kunnanta "ki rinqa duba gabanki idan kina tafiya Mana kada kiyi Mana asara pls". Ya fuske yayi wucewarsa ciki Bai Kara bi ta kanta ba. Nan inda ya barta Bata iya motsawa ba, wani Abu ilahirin jikinta keyi itafa ji take kamar kafarta bazata iya daukar ta ba wallahi,.shi Kuma wanene wannan a tare da malam haka? A Ina ya Samo shi Dan a gaskiya baiyi Kama da kolo ba Sam to waye shi?". Tambayoyin dake Mata Kai kawo kenan a kwakwalwarta daga ganin mutum haka kawai ze nemi yayi Mata shiga hanci da qudundune,ga wani irin kwarjini a cikin idanunsa da Bata taba gani a gurin wani namiji ba. Bata ankara ba taji maganar malam Baba Yana fadin " A'a Fatimah ya Kika tsaya a Nan ko wani Abu kike jira?" Da sauri ta bude idanun tana kallon malam da wani yana binsa a bayan. "A'a ba komai Daman gurinka zani jikin Iya Abun ne Naga kamar ya Dan matsa tana ta rawar sanyi". Ta fadan kanta na kallon kasa kamar marar gaskiya, dan ji take kamar malam din Yana Jin mayen kamshin turarensa da ilahirin jikinta keyi. "To Babu laifi muje ciki, yanzu Mahmud yaje ya dauko abokinsa don ya kara dubata tunda jiya sunje Asibiti da Halima matar malam Mudi ance zazzabin typoid ne yake damunta, to da jikin yaki Dadi ne za'a Kara bincike ko na cizon sauro ne zazzabin".. suka wuce ciki sannan zahrar tabi bayansu zuwa falon Iya Abun Kamar kazar da kwai ya fashewa a ciki. Yana tsaye daga bakin kofar ta waje ya harde hannuwansa a kirji kamar Mai tunanin. Ganin malam din da salahuddeen sun shigo ya daga kansa Yana amsa sallamar su. Mujiba ce ta leko tana fadin" ta tashi din gata Nan fitowa". Bai shiga falon ba Saida malam ya Fara shiga sannan suka biyo bayansa. Sannu salahuddeen din yayi Mata ya dauki jinita take a Nan yayi Mata gwajin maleria ai kuwa ita ke damunta har ta Kai || +. Allura ya dauko Yana fadin " malam allura za'a yi Mata emal, idan Allah yasa an dace shi kenan idan Kuma Bai sauka ba sai ayi Mata Attusunate, amma muna fatan Allah yasa a dace ma". "Allaumma amin ya Rabb". suka fada su duka. Magunguna ya rubuta Mata na ulcer da tayi masa complain na ciwon girji da gefen kafadar ta, sannan yayi Mata Allah ya sawaqe suka fita. Har magariba su zahra suna gidan Baba malam, tun bayan fitar su malam ba dadewa Iya Abu ta koma daki ta kwanta Zahra ta rufeta da wani qaton blanket barci Mai nauyi ya dauketa. Nan falon suka zauna suna Dan tattaunawa da junansu, da tafiya zasuyi Majiba tace su zauna zuwa wani lokacin tunda ansan suna Nan Dan lokacin da zasu shigo mujibar taga kaninta Mubarak tace ya fadawa Mama suna gidan Baba malam. Duk hirar da Mujiba ke yiwa Zahra Sam hankalinta baya tare da ita ta tafi duniyar tunanin abinda ya faru dazu da Wanda aka Kira da Mahmud wai ita Zahra ce kwance a kirjin wani namijin daba muharraminta ba, Kuma ba wani mataki data dauka Koda kuwa na kad'a Masa warning ne yanda gobe baze Kara marmarin rungumar wata ba, Amma Wai sai gata ta b'ige da shakkar idanunsa abinda kaf tarihin rayuwar ta hakan Bai taba faruwa da ita ba, ga wata faduwar gaba ta ba gaira ba dalili data sameta yanzu, ganin nan biyu da tayi Masa duk Abu daya takeji a kansa. Wani wawan tsakin Zahrar tayi Wanda ya tabbatarwa Mujiba Bata tare da ita duk zubar da takeyi kamar 'ya'yan kanya. "Keda waye kike tsaki haka kuma?". Majiba ta fada. "Kedai kawai bari kawai ba komai. Ta fadar tare da you kwafa ta tashi tsaye tana fadin "Tashi mu wuce gida tunda Naga wannan barcin na Iya Abu bana Kare bane, inaga har da allaurar barci yayi Mata gaskiya". A kofar gida suka yiwa malam sallama Yana ta Sanya musu Albarka. Tun daga ranar Zahra Bata sake fita ba tana gida saidai lokaci-lokaci Mujiba na shigowa, a ranar data cika sati daya Abbansu ya dawo murna ba'a maganarta gurin Zahra, duk da tana ganin shi a can syprus din idan yaje Amma hakan bai Hana sun Kai wani lokaci ba suna tattaunawa irin ta d'a da mahaifi. Saida Zahra tayi sati biyu sannan ta nufi Jos gurin Aunty Hasana. Taji matukar dadin zuwanta Jos din. Dan har gidan Aunty Jana sukaje da Yara tunda lokacin da akayi bikin Bata Nan. Duk inda ya kamata taje taje har gidansu Mama taje haka ta kaiwa jannifer ziyara lokacin sunyi hutu tana karatu a Nan University ta Jos. Maganar samari da gaske ta sakata side idan ka ganta tana magana Mai tsawo da namiji to ka tabbatar dan uwanta ne ko wani Mai qirma a idanunta. Satinta daya a Jos suka taho tare da aunty Hasanar da Yara Wanda a satin sukayi hutu, bayan dawowar ta daga Jos ne su Hameeda sukazo hutun semester. A lokacin ne Salma ta fito mata a mutum sak, ta nuna da gaske Bata yin zahra abinda yaso ya kawo b'araka Mai girma kenan tsakanin Mama da Ammah Dan da gaske an Kai hakurin Ammar karshe, maganganu Salmar ta ringa saki kamar lokutan baya, sai dai a wannan karon Zahrar ta nuna Mata jiya fa ba yau bace, idan da tayi tolerating na nonsense din ta a yanzu Kam dai dai take da ita tunda Bata Jan girmanta a gurinta, abinda ya Kara harzika Salmar lokacin da Zahra ta kalleta tayi tsaki tace "Wai wannan ce mace,kina duba mirror Kuma kina ganin kanki kuwa?gara ni da har kike min gorin ana saka aurena ana fasawa, Ina laifi tunda har ana ganina ana sona, kaddarar Babu mijina a cikin su ce take rabani dasu, kefa ko Kare Bai taba zuwa yace Yana sonki ba, baga kanwarki Nan ba Ina cewa har anzo tambayar aurenta? kije kiji da abinda ya dameki Zaki zauna kina fada da kanwar bayanki". Tana Gama fada Mata maganar ta nufi hanyar ficewa daga dakin. Cikin fushi salmar tayo kan Zahrar ta fardota baya saura kadan ta Fadi dai dai lokacin Kuma sahura ta shigo zatayi musu sharar yamma ta tarar da wannan badakalar, da sauri ta shiga tsakanin tana Basu hakuri ta Kama salmar ta fita da ita daga dakin tana faman zagin Zahrar abinda ya janyo hankalin Amma dake main kitchen din gidan tana yiwa Abba gas meat saboda Yana sonsa sosai yawanci idan Yana gida kusan duk dare sai anyi Masa shi. Da sauri ta fito tana tambayar "me yake faruwa ne?" Sahura ce ta fada Mata abinda ta shiga ta gani tsakanin Zahra da salmar, juyawa kawai Ammah tayi ta koma taci gaba da aikinta Bata Kara lekowa ba tanaji Mama ta fito tana fadan daman ai ba tun yau ba ta fuskanci Zahra ta Raina Salma, Kuma komai runtsi dai Salma ai gidan ubanta ne Nan ba Mai hanata sakewa. Zahra ce ta fito zata wuce zuwa part din Ammah,har ta gota Mamar batace komai ba, Mamar tace. "To fiqe kafi qaya tsini da Kika Samu guri kina yanda kikeso a gidan wallahi duk rintsi bazaki Kai matsayin 'ya'yan gida ba, tunda har abada ba'a canzawa tuwo suna" Har zahra tayi kamar ta maida Mata martani sai taji bazata iya ba babba babba ne, kawai ta shige part dinsu. Har Mama ta juya taji maganar Ammah daga bayanta, dan harga Allah batasan Ammah ta fito main kitchen din ba, Sam duk da tana jiyo kamshi ta dauka a can part dinta take aikin. Bata juyo ba Amman ta tsaya. Ammar tace "Haba Mama ban zaci haka daga gareki ba wallahi, cewa nake da Zahra da su Hameeda dauka daya ne a gurinki, ai saiki tambayi meya hada fadan?kiyi musu fadan gaba daya ba wai ki nuna Salma itace taki ba, kina fadin maganganu irin haka ai na dauka ni duk binda lauje ya yayo a gidan Nan ya kamata ki dauke shi ciyawa ne na gode amman ki sani Banda komai nufin Allah ne Zahra tafi karfin ace Mata 'yar karere tunda Mai gidan ne da kansa ya karbo rikon lokacin da aka nemi tafiya da ita kema Kuma sheda ce kinsan su waye kakanninta ba bakinki bane, dukiya idan ana gadonta kinsa Zahra 'yar mun gada ce, ko shi Wanda kike takama da dukiyar tasa yasan tazarar da nisa a tsakaninsu da kakanninta idan kina tunanin karya ne idan yazo ki tambaye shi ze Baki cikakken bayani". Bata jira taji abinda mamar ke kokarin fada Mata ba tayi gaba abunta ta nufi part dinta. Tun daga ranar Ammah ta daukewa Mama wuta gaisuwa kawai ke hada su, a kwana na biyu da Mama ta karbi girki ta kasa hakuri ita abin yafi damunta ta fadawa Abban Ammah Bata Mata magana, yayi mamaki matuka da gasken gaske Dan wannan shine karo na farko da irin haka ta faru da matan nasa duk tsawon shekarunsu. Bai taba rabasu akan sun Sami matsala ba Koda wasa, dan haka ya Kira Ammah a waya yace tazo part dinsa Yana son ganinta. Batayi mamakin ganin Mama a zaune ba tasan za'a Rina tunda kaf tasan halin Mama na zahiri. Gaishe da Abban tayi suka Kuma gaisa da Mama, tambayar ta Abban yayi ko akwai abinda ya hadasu da Ammah ne?. Ba wani kwana kwana ita Daman tun can baya Bata da munafurci ko kadan. Dan haka ba wani ta fadawa Abban duk abinda ya faru tunda Saida ta tutsiye Zahrar akan ta fada Mata abinda ya hadasu da Salma da kuma abinda mamar ta fada, shi kanshi Abban yayi mamakin abinda Salma tayi sosai, itama Mamar ya nuna Mata kuskurenta na fadar wannan maganar ya Kara da cewa. Ban tabi yiwa zahra kallon ba nine na haifeta ba, bil hasal ma shine dalilin da yasa ban aura Mata Daya daga cikin 'ya'yana ba, ita kadaice ba uwa ba uba tun batasan inda kanta yake ba, mu ta sani a matsayin iyaye sauran yaran Kuma 'yan uwanta. Idan na aura Mata wani a cikinsu ba zata Zama feel free tare da ni ba, idan damuwa ta shiga ba Wanda zata fadawa kinga ai anyi adoh badan kyau ba". " Haka ne suka fada. "To karna Kara Jin makamanciyar irin wannan maganar, ba Wanda ze kawo min rarraba kan iyalin gidana. Zahra 'ya tace kawai na saka sunan mahaifinta ne Dan haka shari'ar musulunci tazo dashi, badan in nunawa duniya bani na haifeta ba, a kiyaye kodon gaba". "In Sha Allah". Suka fada. Bayan tafiyar iyayen yasa suka turo yaran yayi musu fada sosai sanan ya Kare da nasiha. Tun daga lokacin abubuwa na zahiri sukayi sauki sosai. Kusancin Zahra da Hameeda ba abinda ya taba shi saima Kara shakuwa sukeyi a kullum suna Jin dadin butun, Zahra suna waya sosai da Ummee da Mama Hanifa harma da uncle Haisam a wasu lokutan. Lokacin da hutunsu ya kusa karewa duk sai Zahra ta nemi walwalarta ta rasa ko da yaushe kamar marar lafiya ana saura kwana biyu ta tafi Ammah ta matsa Mata taje Kiran da Baba malam yake Mata, dan sau kusan uku yana turo Yara tana cewa gata Nan Amman sai tayi burus da zancen. Har dai ta Kai Ammah karshe tayi magana. Hameeda tace ta rakata suje tare, yau gurin malam din ba kowa ba Kuma rumfar karatu tunda ranar basa karatu. Gurin ganawa da mutane suka sameshi su Habib suna ta gyaran Shirin kantar littafai. Da sallama suka shiga suka gaishe da malam din sannan suka gaishe dasu Habib, sai sukayi shiru. Malam ne yace "Zahra'u Ashe lokacin komawar taki har yayi ko?" Kara risinawa tayi tana fadin "eh lokacin yayi yayi Baba gobe zan tafi in Sha Allahu amma a Istanbul zan tsaya sai wani satin zan wuce syprus din". "Masha Allah. Allah ya taimaka, ki Kara hakuri akan lamuranki duk wani bawan Allah na kwarai sai Allah ya jarabce shi Dan ya gwada imaninsa ki dauki abinda yake faruwa dake Daman haka Allah ya rubuta Miki taki kaddarar kada ki yanke kauna daga Rahamar Ubangiji. Ga addu'oi nan da littatafan addu'a ki tafi dasu ki ringa yinsu Kuma kada a shagala da ambaton Allah a duk inda aka Sami kai, Allah yayi Albarka ya bada nasara ya kiyaye hanya". "Allahumma Amin suka fada a tare". Habib malam ya yiwa magana ya Miko ledar da aka saka sakon nata, Hameeda ta karba suka Kara yiwa malam godiya suka fito suka shiga cikin gidansa Zahra ta Kara duba jikin iya Abun ta Kuma yi Mata sallama. Basu koma gida ba, gidan su mujiba suka shiga Bata Nan ma sai Maman ta suka barwa sallahun tafiyar zahrar suka nufo gida, sunzo dai dai masallacin gidansu ne sukaga Ya Abdul Hakeem da Dodon Zahrar a zauna a kan carpet karami a gefen masallacin suna hira Kai da gani da kyakykyawar alaqa a tsakanin su. Gaishesu sukayi suka wuce, Hameeda ce ta kalli Zahra tana fadin "Kinga wancen Guy din yanda Salma ta mutu kansa ba magana! lokacin data Fara ganinsa munzo hutu wallahi kamar zata zauce akansa sai da Mama ta taka Mata burki taci Mata mutunci akan ta rasa Wanda zata so sai Almajira Wanda ba'a San asalinsa ba, duk yanda taso ta nunawa mamar wannan da banbancin da irin Wanda ta sani amma Sam taki fahimta Dan har so tayi tayi Mata duka tana fadin Dan lalacewa ta rasa Wanda zataso sai fakiri Mai allaziwahidin Dan salon Abba yaji ya Goya Mata baya tunda Wai ance sune suka kawo shi garin bandai San kan labarin ba gaskiya". Ita dai Zahra Bata tofa tataba daga uhm sai umh umu uhm, har suka karasa gida. A Daren sun raba dare suna Hira da Ammah a Nan ta dunga yi Mata magiyar ta daure taje gurinta ko zuwa karshen shekara ne ta ganota ba ta tura Mata Ya Abdul Hakeem ba. Karfe shida Mai kyau sun dauki hanyar Kano ita da Ya Abdul Hakeem da Hameeda da magaji. Nan suka zauna da zahra suna ta Hira kafin lokacin tashin su yayi, in da wani Abu da ya damu Zahra a gurin Bai wuce kallon da wani matashi ya kureta da Shi ba, duk inda zata dago Kai sai sun hada Ido dashi, Sam ya hanata sakat da idanunsa idan ba idanunta kemata gizo ba har wani lumshe ido yake da wani kankance su. A haka har lokaci ya cika aka Fara shiga jirgin hand bag ce kawai a hannun Zahra tunda kayan an tafi dasu tun zuwansu lokacin da ta juya ta Fara tafiya ba zato taji hawaye a idanunta abinda ta dunga kokarin kar tayi kenan tun daga gida lokacin da Auta Musaddiq ya fasa Kuka da suka taso Amma sai gashi ta kasa jurewa itama Saida suka zubu, juyawa tayi kadan lokacin da zata hau steps din sai taga Ya Abdul Hakeem ya Kama hannun Hameeda sun juya sun Fara tafiya tana share hawaye da dayan hannun itama ta juyo hannu Zahra ta dago Mata alamar bye sannan ta Haye zuwa ciki. Kusa da wata Mata ta zauna da alamar kamar zatayi sa'ar Ammah, ta gaisheta. Saida jirgin ze tashi ne taji na gefenta Yana fadin "duk tunanin gidan ne ya hanaki jin sanarwar a daura belt da ake ne?" Ya fada in a soft voice. Dago Kai tayi ta dubi Mai maganar dake gefenta, wannan Wanda ya dameta da kallo ne kafin su shigo, ita Sam batama San sanda ya zauna kusa da ita ba. "Nagode" ta fadawa tana saka belt din lokacin da jirgin yayi balance a sama ne ta cire belt din ta bude computer dake jikin kujerar dake gabanta tana kallon location din da Suke bi tun tana Gane garuruwan data sani ko take jin sunansu har aka shigo Wanda sai dai ta karanta kawai. Jefi jefi suna Dan magana da matar dake kusa da ita. Nan kusa da ita dai Bata Kara kallonsa ba tunda taga shi kallon mutane kamar dabi'arsa ne. Sanyi kamar tafiyar awa daya taji yana Mata magana da farko yi tayi kamar bataji ba, Saida matar dake kusa da ita tace "bakyaji ba ana Miki magana, ko kina da aurene?". Kai ta girgaiza alamar A'a. "To meyasa kina Jin Yana Miki magana Kika kyale shi? ba Dadi irin haka baka wulakanta mutum ba kasan gaba abinda Allah zeyi ba kinji". A hankali take Mata maganar yanda ita kadai zata iya ji. "Tom nagode in Sha Allah zan kiyaye". ta fada mata. Bai hakura ba har Saida ya Sami kan Zahra duk da ba wani sakewa tayi dashi ba Amma dai hakan yayi masa. Lokacin da suka sauka haka ya dunga bin Zahra kafa ya kafa har ta dauko kayan ta da aka gana screening suka fito, a Nan ya fada Mata sunansa Mushahu shi Dan Kano ne Yana aikin government Yana Kuma kasuwwnci yanzu ma harkar kasuwancin ta kawo shi kasar. Zahra ma ta fada Masa sunanta da inda take karatu da Dan zaman da zatayi anan kasar kafin ta wuce. Bai bar airport din ba har Saida Mama Hanifa tazo daukar zahra, da yake Mushahun wise ne sosai ya sake da Mama Hwnifar don Basu rabu ba har Saida ya karbi address din gidanta, saida suka bacewa ganinsa sannan Shima ya nemi taxin cikin airport ya nufi hotel din da yake sauka idan yazo kasar da buri kala kala a zuciyarsa kan Zahra. Satinta daya ata nufi syprus kafin lokacin Mushahu ya Kai Mata ziyara yafi sau hudu ba karamin samun shiga yayi a gurin Mama Hanifa ba. Zauwanta makaranta da kwana daya Sajida da Khadijah da Fatima suka dawo Anisa ce Bata dawo ba suna Umara da Yayarta sai Kuma sukayi Dan Samu matsalar visa. Karatu Suke ba Kama hannun yaro Koda yaushe suna busy da karatu, tunda Zahra ta rabu da Musbahu a turkey Sam ta aje batunsa a gefe duk da kusan Kullum saiya kirata sun gaisa Yana ta kafa gwamnatin sa a gurinta. Bazato ba tsammani ranar wata Saturday taje weekend gidan Uncle Haisam ya kirata da number din kasar Yana fada ya shigo kasar tayi jiransa Nan da awa daya ze shigo makarantar, ba karamin mamaki tayi ba da jin hakan, dan harga Allah batayi zaton da gaske yake ba da yace Mata Yana Nan zuwa syprus din. Nan da Nan ta fadawa Aunty Jinan matar uncle zata koma school yau suna da wani group Assignment data manta zasuyi ta taho, Bata Hana ta ba tunda Daman uncle din baya kasar sunje wani aiki south Korea, snacks Aunty jinan ta hada Mata masu yawa ta tafi dasu. Allah ya taimaketa ta fito da card dinta na shiga bus ko train, mintina talatin masu kyau suka kawota kyrenia city. Lokacin data shiga hostei dakinsu ta wuce ta Kara gyara jikinta. Wani karamin basket da dauko ta zuba snacks da drinks masu sanyi, turare ta Kara fesawa har Brandy wadda Suke daki daya take tambayar ta ko zataje wani park ne ta huta yau weekend? Eh kawai tace Mata tayi gaba ta fita daga dakin, gurin su Sajida ta nufa akayi rashin sa'a duk basa Nan sai Anisa kawai ta Samu tana sallah. Zama tayi tana tunanin yanda lamura Suke ta juya Mata kamar a almara ko wannan din shi ya zata Kaya a kansa? Dan haka Nan taji bazata iya yi Masa rashin kirki ba Dan duk Wanda ze Bata kudinsa da lokacin sa ya biyoka har wata kasar duk da baka bashi fuska ba to kuwa Bai cancanci wulakantawa ba a gurinka. Kafin Anisa ta idar da sallar wayar Zahrar tayi Kara alamun Kira ya shigo, number dazu ce ta daga tayi sallama, daga can ya fada Mata ya shigo ciki da inda yake. Bayan sun gama wayar ne Anisa ta idar da sallar ta kalli Zahrar tana fadin "yaushe Kika dawo nayi zato sai Monday da safe Zaki dawo?". "Ke dai Bari kawai wallahi guy din Nan Dana fada muku mun hadu a airport din Kano Yana kallona har ya bini gidan Mama Hanifa?" Kai Anisa ta gyada alamar ta gane. "To shine fa dazu ya kirani Wai gashi a kasar ya cika Alkawari zuwa anjima ze shigo Nan gurina, shine yasa na dawo yanzuma kiransa ne ya shigo Yana gurin garden din can na gurin second gate". A gurin suka same shi Yana tsaye kusa da wani kangaroo na siminti Yana kallonsa har da kanana a kusa dashi yayi kyau sosai kamar na gaske, ya shagala da kollon har baisan sunzo gurinsa ba Saida Anisa tayi Masa sallama sannan hankalinsa ya kawo kansu. Wani irin mahaukacin kyau yaga Zahrar ta karayi a idonsa, kasa dauke idanunsa yayi daga kanta. "Masha Allah!" Ya furta a hankali Yana fadada fara'a akan fuskarsa tare da amsa sallamarsu. Karkashin wata bishiya Anisa ta nuna masa inda akayi kujerun sumunti masu kyau sosai, bayan sun zauna ne Anisa ta gaishe shi tana Masa ya hanya, sannan Zahra ta gaishe shi itama, duk sai taji duk wani iri saboda Sam lamarin maza gaba daya ya Gama fuce Mata daga Rai duk da bazata ce sun yaucareta ba Amman lamarin su a gurinta Mai girma ne Dan duk yanda taso ta manta abunda ya faru a baya Bata iyawa, Samun kanta tayi da wani irin Jin bazata iya watsa masa kasa a ido ba. Sun jima suna tattaunawa da Anisa a fakaice Yana yiwa kansa campaign a gurinta, Anisar ta gabatar Masa da abubuwan da suka kawo masa, ita dai Zahra tana jinsu suna ta Hira kanta na kasa tana Dan Wasa da wani zoben white gold da Aunty Nawwara ta saya Mata lokacin da sukaje Umara. Anisa ta jima sosai kafin tace zataje ta duba idansu Sajida sun dawo. Bayan tafiyarta Musbahu ya yayi duk yanda zeyi ya janyo hankalin Zahrar ta sake dashi Kuma Alhamdulillahi kafin wani lokacin ta Dan sake ba kamar lokacin da suka zoba, a nan yake fada Mata shifa da gaske yakeyi yafi son kafin ta Gama makaranta a Gama komai tana gamawa kawai ayi bikin tayi service a gidansa. Saida aka dauki lokaci sosai sannan su Sajida suka karaso gurin bisa jagorancin Anisa, sun jima suna Hira sosai anan yake fada Mata Shima Dan kano ne sokoto road, ita Kuma ta fada Masa tana Jambulu Amma da suna zaune a Gwammaja ne. Ya jima sosai kafin ya tafi,washe gari Sunday yaso su fita Amma Zahra ta nuna ba wannan maganar duk yanda yakai da naci ta Kiya har su Sajida suka saka Baki Amma ta qiya. Satinta daya ya koma inda ya sauke Mata kudaden masu yawa ya Kuma yi Alkawarin gabatar da kansa gurin iyayenta tunda bada Wasa yazo ba, itama Kuma Bata Hana ba tunda da gaske taji yes zata iya rayuwa dashi idan Allah ya amince. Bayan barowarsa kasar da sati daya ya gabatar da kansa ga Alhaji Jafar a matsayin Mai son auren Zahra, Bai rufe Masa komai ba har zuwan da yayi syprus din,sai dai ya bashi hakuri akan zuwan daya Farayi kafin yazo gare shi, ba komai Alhajin ya nuna masa sai dai yace irin hakan bashi da kyau kodon gaba mutum yabi 'ya mace wata uwa duniyar batar da sanin magabatanta ba akwai hadarin lalacewar tarbiyya ga Wanda Allah yasa shaidan yafi karfin zuciyar su. Alhajin yayi Masa tambayoyi sosai akan Sana'a da Kuma asalinsa, sannan ya fada Masa shima mahaifinsa ya rasu tun Yana level one hundred a jami'a, a labarinsa daya fada masa nan ya gano kanin mahaifansa sunyi makaranta tare dashi a Bauchi. Bayan tafiyar Musbahun da Alhaji Jafar ya tada mutum takanas yaje har Kano da taimakon abokinsa Alhaji Muttaqa akayi Masa bincike kan Mushahu Kuma Alhamdulillahi ba'a Sami wani abun ashsha ba a tare dashi Dan mahaifiyar ma ta fito ne daga cikin manyan gidajen sarautar Kano. Bangaren Zahrar kuwa kusan Kullum suna tare da Musbahun a waya Dan har ya haddace lokacin agogon kasar, tun tana daridari har ta sallama tare da karfafawar su Sajida kafin su gama semester din sun shaku dashi sosai Bata rufe Masa matsalar data fuskanta a baya ba, nuna Mata ma yayi rabonsa ne ya kawo aka ringa samun akasin na bayan ya Kuma yi Mata Alkawarin ruwa da iska ba abunda ze girgaiza tarensu bare har akai ga rabuwa Koda kuwa Aljani ne ya aurata in sha Allah sai yaga bayansa, yayi Mata alkawura da dama ya nuna Mata Babu wani abu da ze girgaiza shi koya bashi tsoro akan lamarin aurenta. Magana tayi nisa Dan har iyaye sun shiga abinda yayiwa Ammah Dadi kenan Dan wannan karon Kam Zahra tayi Dace da Dan manyan mutane sosai, dan basu bar garin ba Saida suka shaida lokacin aure idan ta gama service da wata daya duk da sunso ayi bikin kafin tayi service din sai Alhajin ya nuna musu suyi hakuri tayi idan ta gama saita zauna guri daya ba daga kaita ba ba dadewa ta Fara fita kullum, Kuma ya Hana kayan lefe Dan Alkawari yayi ankawo biyu an karbe to kuwa ko waye zata aura sai dai ya aje Mata kayan idan taje gidan ya Bata. Lokacin dasu Zahra suka Gama karatunsu har da Ammah da Hameeda akaje bikin graduation dinsu mutanen Jordan ma sunje har Mama Hanifa. Bayan kammala taron sun Kara kwanaki a kasar, Zahra ta raka Hameeda kuraren shakatawa da yawa tayi kallo tayi santin inama Abba ya dawo dasu Nan Suma gashi ita har ta Gama Amma su Kullum karatunsu ba cigaba ana faman strike tunda a yanzu ma shine ya dawo dasu gida har ta samu damar zuwa itama. Ranar da zasu taho sun Sha kukan rabuwa dasu Sajida tunda su saura shekara daya su gama. Murna gurin Zahra ba magana ji take kamar ta sauke wani abu Mai nauyi daga kanta. Musbahu yaso zuwa graduation dinsu Zahrar Amma lokacin Yana busy yaje wani special assignment a Kenya dole sai hakuri yayi, Amma Yana dawowa ya yiwa Azare dirar mikiya a ranar Zahra taga zallar so a gurinsa Dan ji yake kamar ya dauke ta yayi gaba da ita, itama ta bashi kulawa kamar me,Hameeda tazo sun gaisa sun Dade suna Hira dashi tambakar sun shekara da sanin juna, sunan mujiba ma ta shigo suka gaisa ba shi yabar Azare ba sai kusan magariba Dan ma Zahrar nata Masa magiyar ya tafi saboda rashin tsaro irin na kasar. Tun daga lokacin hanya ta aure shi tsakanin kano da Azare. Mushahu na mutane ne kusan duk Wanda ya kwana ya tashi a Nan kukkuken unguwarsu Zahra yasa shi Koda kuwa ba gaisawa suke ba, wata kila ya taba yiwa wani alheri a cikin yaran gidanku Dan da gaske hannunsa a sake yake gurin Alkhairi. Sunyi sabo sosai da jama'a a Nan har gurin malam Bukar Yana zuwa sauda dama idan ya shigo garin, wasu ma daga cikin samarin gidan malam din sunyi sabo sosai. Lokacin da results dinsu Zahra ya fita Sam bataje ba Auncle Haisam ne yayi Mata komai Allah ya taimakeka ta fito da first class degree a akan anatomy. Allah ya taikata da taimakon Ya Hassan aka kawota bauchi service, bayan zaman camp sukayi posting dinta Dr Sulaiman Adamu memorial college of Hygiene and Environmental health science Azare. Ammah taji dadin hakan sosai haka shima Mushahun yaso hakan kwarai da gaske. Zahrar najin dadin aikin sosai da sosai domin teaching Yana cikin hobbies dinta. Bayan sun Gama ne da wata daya kamar yanda akayi Alkawari aka Fara kokarin Fara shidimar bikin ta dai dai lokacin Kuma akayiwa su Ummee rasuwa a saudiyya abinda ya Hana su zuwa kenan da har Ammah tace a daga bikin tunda rasuwar ta jikinsu ce kanin Baban Ummeen ne ya rasu,Amman sai sukace Dan me ayi idan komai ya lafa zasuzo suga daki kawaii. A satin da za'a Fara bikin kusan Kullum Mushahu da Abokansa shakikai su Deeni da Aliyu Wanda Suke cussings suke ta zirga-zirgar ganin abubuwa sunyi yanda ake so duk wasu programs a nan za'ayi dinner ce kawai zasuyi a Kano, sun Kama dakuna uku a hotel idan zasu zauna har zuwa Daurin aure. Saura kwana biyar Daurin auren ne wani abun al'ajabi ya faru da Hajiya Nafisa Maman Mushahu wadda suke Kira da Ammi. Cikin dare tana barci ta farka a matukar razane saboda wani mugun mafarkin da tayi da Musbahun akan auren, addu'a tayi ta koma ta kwanta ai kamar jira ake barcin ya dauketa sai abunda ta gani a wannan mafarkin yafi wancen muni, wasa-wasa barci ya gagareta a wannan Daren kafin safe duk ta wani hargize ga wasu irin tunane tunane sun cika Mata zuciya na rashin kwanciyar hankali kafin yamma gaba daya ta Zama wata marar nutsuwa ba shiri ta Nemo kanwarta Aunty Jamila a waya Nan da Nan tazo tunda ba aure gareta ba, duk ta kwashe komai ta fada Mata akan Bata son auren Musbahun kwata kwata ita fa ko a cikin ranta ta tuna da zeyi aure ji take kamar zata zauce, da farko Aunty Jamilar ta dauki abun Wasa Amma ganin da gaske abin yake yasa ta Kira Babban yayansu Alhaji sulaiman da kanin Baban su Musbahun Alhaji isma'il, Suma da farko sunyi zaton na Wasa ne Amma da suka matsa akan ta Fadi dalilinta na Hana yuwuwar auren sai abun ya ta'azzara ya Zama kamar Mai tabin hankali, ganin abun Yana neman ya Zama wani iri ne yasa Alhaji sulaiman ya kirawo Aliyu tare da tambayar suna ina?. Aliyun yace gasu Nan a hanya sunje Azare ne Amma har sun wuce wudil sun kusa kano ya fada Masa lallai direct su nufo sokoto road su duka. Haka suka shigo suka tarar da wannan dambarwar ana ta fama da Ammi. Ai tana arba da Mushahu ta Kara tuburewa tana fama fadar wallahi matukar ya kafe sai auri Zahra Bata yafe Masa nononta da yasha. Su dai Basu ankara ba sai ganin Mushahu sukayi ya sulale ya zube a sume, da sauri Aliyu ya kawo ruwa aka zuba Masa Amma a banza ganin haka yasa suka nufi Asibitin Nasarawa dashi. Haka aka dunga juyawa da Ammi Amma ta kafe kamar kafiran farko duk Wanda ake tunanin ze kawo gyara a lamarin an fada Masa Kuma yayi bakin iyawarsa Amma ba wani ci gaba da aka nemi a Zafafa sai lamarin yaso ya koma Mata tabin hankali abinda daya tada hankalin Babarsu kenan Hajiya Yaya tace dole a hakura da auren tunda abin yazo da irin wannan lamarin marar Dadi daman tun farko ita bataso lamarin ba sai dai yaran yanzu ne baka hanasu abinda suke so, tunda Daman fa ance shine na uku a Wanda zasu auri yarinyar ana fasawa to shima gashi tun ba'aje ko Ina ba lamarin ya Zama haka. Tashin hankali iya tashin hankali Musbahu ya shiga Dan dakyar aka Sami nutsuwarsa dan kwata kwata ya daina magana da kowa ya rufe duka wayoyinsa shima Deeni ganin kiran Zahra yasa ya rufe layin da suke wayar da ita, Aliyu ne kawai Bai rufe wayar ba Amma baya picking idan ta Kira a halin hake ne su Alhaji sulaiman sukaje Azaren da labari marar Dadi Wanda ya kawo karshen 'yar Wala walar da akeyi da Zahra akan aure ta kawo karshen duk wani makirci da bita da kulli da ake Mata na rushe aurenta idan ya taso abinda ya girgaiza duniyar Wanda suke fake suna tsula ta'addanci ta karkashin kasa. ✨ ✨ AUREN HUCE HAUSHI ✨ ✨ MAMAN FATIMAH Assalamu Alaikum warahamatullahi ta'ala wabarakatuhu. Dan Allah ayi hakuri da matsalar da aka samu gurin turo page fourteen sau biyu hakan ya faru ne saboda wasu dalilai Amma na karshen Wanda na turo shine cikakken fourteen din yanzu kuma na hade fifteen & sixteen guri daya na gode. Page Fifteen & Sixteen 📖🖋️ BACK TO STORY. ________ Gurin Zahra su Sajida suka shiga tana kwance a gado idanunta a rufe tayi zurfi cikin tunanin, Sam bataji shigowar su Sajida ba Saida mujiba ta Dan zungure ta bude ido ta yunkura ta tashi zaune tana dafe kanta dake Sara Mata. Sajida ce ta zauna kusa da ita ta Kama hannun Zahrar tana fadin "bestie Dan Allah ki rage tunani kada wani ciwon ya kamaki, ki yawaita addu'a komai yayi zafi maganinsa Allah. Kuma wani hanin ga Allah baiwa ne, ke kanki Baki taba tunanin abun ze Zama haka ba, Kuma Allah ya juya lamarin yanda yaso, to saiki gode Masa bisa ni'imar da yayi miki, Kuma nifa mujiba Ina doubting akan wannan da aka daura musu aure, Kuma ki rubuta ki aje zakice na fada Miki kije kiga gidan da za'a Kai bestie, Kuma ki duba kiga irin kayan da aka kawo yanzu kinsan duk Wanda ya hadasu first class ne a gurin gayu wallahi komai bana banza Amma Kuma Wai almajiran malam ne gaskiya I doubt much". Ta fada tana kallon mujibar. Ita dai Zahra ta rasa inda zata Kama komai ya kwance Mata, su damuwarsu kaya da gida, ita Kuma tata damuwar ta yanda za'ayi zaman ne, har yanzu gani take kamar a mafarki Wai wannan karon ma Saida aka samu akasi,ta rasa daga Ina matsalar take, shi kuma auren da aka daura meye ze biyo baya tasan idan ba wani nufi ba na Allah shima sai an Sami wani kalubalen a cikinsa. A hankali ta furta "Ya Salam! Allah ka shiga cikin lamarina, wallahi bestie komai ya kwance min bani da sauran dabara,kwakwalwata ta daina aiki yanda ya kamata kinsan Allah nifa kamar ma tsoronsa nakiyi Dan tunda na Fara ganinsa naji wani irin Abu a jikina wanda ban tabaji ba a kan ko wane namiji sai shi, Kuma yayi min abinda ya kamata na dauki mataki Mai karfi amman wallahi ko magana kasayi Masa nayi, yanzu kuma a haka zan rayu dashi? Ni wallahi bana sonsa Sam Kuma fa Shima yace baya son abin yake ba kawai dai baze iya watsawa su Abba kasa a ido bane". Ta karasa fada hawaye na zubo Mata a fauska. Lallashinta sukayi da kyar tayi shiru kafin mujiba tace "haba Zahrar ki daina kuka idan kina daga hankalin ki na Ammah ma baze kwanta ba, Kinga irin haka ba Dadi duk da an aura miki Wanda babu soyayya da shakuwa a tsaninku, ita a hakan ma yayi Mata da ace wannan karon ma an fasa aure gara hakan tunda naga alama da ita ake fadan ke kin ratso ne kawai ake fakewa da lamarin ki Dan a Hana duniyar ta zaman lafiya da kwanciyar hànkali, Kuma Baki san dalilin da yasa Abba yayi hakan ba, kinsan dai Abba baze taba aura Miki baragurbi ba kedai kiyi ta addu'a muma muna tayaki, Bari na tambaye ki Mana idan kina addu'a bakya cewa Allah ya Baki miji na gari?" Hannu tasa tana share guntun hayenta kafin ta harari mujibar tana fadin "Ina yi Mana kuma kawai saina yi sallah na kasa wannan addu'ar dan na Zama abinda na zama ko?" "A'a ba haka nake nufi ba bayani zan miki shi yasa nayi Miki tambayar dai, Allah ya huci zuciyar Amarya". "Kina jina mu 'yan adam muna rokon Allah ya zaba mana abinda yafi Mana Alkhairi Amma wani lokacin inda kake zaton alherin ne to sai kaga ba'a Nan yake ba, idan yazo ta inda baka zata ba tunda bakasan gaibu ba, sai kayi watsi dashi idan bakayi sa'a ba haka abun ze kwaranye baka mori komai ba, alhalin Kai ka roka aka baka sai kuma ka Raina abinda aka baka ba tare da kasan shine alherin ba. To Dan haka nake so ki yiwa Allah da manzonsa ki rike abinda Allah ya Baki tunda shi Kika roka Kuma ga abinda ya Baki sai kiyi ta Tahamidi ga Allah kawai, ki nemi Allah ya saka muku kaunar junanku da soyayya da jinkai. Dan kinsan dai idan ba wata kaddarar Ubangiji ba Babu abinda zesa ya rabu dake tunda ya karbi auren Nan wallahi ko rantsuwa nayi bazanyi kaffara ba yana so, dan haka ki daure kiyi Masa biyayya shi arziki nufin Allah ne, naji ana ta 'yan kananun magamganu ki toshe kunnenki kada ki bada barakar da wani ze kushe Miki miji dan bashi da kudi, Allah ne Mai azurtawa lokacin daya so sai kiga wata Rana sai dai a tada labarin abun". Sun Dade suna kawo Mata misalai da yawa na irin wannan auren nata daga baya Kuma ya Zama Alkhairi. ********** A matukar gajiye Mahmud ya shigo cikin gidan misalin karfe biyar na yamma tun safe ya kebe kansa a dakin daya Kama na hotel yake ta faman aiki yaso kwarai ya Gama da wuri kafin yamma amma abun ya gagara Dan da gaske aikin ya dauki hankalinsa sosai ga tafiyar dake gabansa Banda Allah yasa wasu abubuwan sun daidaita a jiya da dole tsakanin gobe da jibi dole yabar garin ko baya so. Amma cikin taimakon Ubangiji sai komai ya Fara daidaita, shi kanshi Yana Jin idan ya tsallake ya tafi daidaita wanna gabar Bai kyauta ba Sam, dan jama'a zasuga kamar ya gujewa auren gatan da akayi Masa ne ya watsa musu kasa a idon an Masa gata irin wannan sun dauki yarinyar su Mai tsada sun bashi ba tare da sun San ko waye shi ba, ko la'akari da karancin samunsa suka aura Masa. Su Habib ya tarar a falon Yana karatun Alqur'ani, Abubakar Kuma Yana ta faman hada Nile sat. Su duka suka amsa Masa sallamar Nan falon ya aje jakar laptop dinsa abinda bai taba kwatanta zuwa da ita ba kenan Dan duk aikin da zeyi sai dai yayi acan hotel din ya barota, amma yau dole tasa ya taho da ita nan saboda so yake ya raba dare Yana aiki shi yasa ma Kai tsaye ya nufo gidan da ita yasan bashi da matsala dasu duka biyun. Abubakar ne ya tsaya da aikin Yana kallon Mahmud Yana fadin "Dan Allah Ina ka shiga Wai bakasan kana dagawa Baba malam hankali ba? shifa yafi son daya juya ya ganka, gashi ka Kama ka rufe wayar ana ta Kira a rufe". Girarsa ta daman ya dan shafa kadan kafin ya zauna Yana fadin "cool down Mana my man Ina kake tunanin zan tafi? Wallahi aikine yayi yawa na wannan NGOs din bakaga har kayan aiki suka bani ba tun zuwan da sukayi wancan karon, yanzu haka ana koya min yanda zanyi amfani da ita laptop din ne yanda zanji dadin aikin, Bari nayi wanka sai muje gurin Baba malam din nayi Masa bayani yanda ze fashimta, sunce ma nan da sati daya ko biyu zasu kiramu zuwa babban taro da za'ayi". Tunda ya Fara magana Habib ya dakata da karatun da yakeyi yana bin Mahmud da kallo haka nan kawai yaji Kamar ba gaskiya Mahmud din ya fada musu ba, Kamar yana boye wani Abu, shifa tun lokacin daurin aurensa ya lura da yanda Kamar yake baiwa Sameer umarni a wasu lokutan sai idan ya farga ne yakan yi maza ya canza taku, sannan a watannin baya ya taba jin yana waya a kusa da dakin da suke taron abinda ya shafi makaranta lokacin yana duba wasu sabbin forms da aka kawo na Enterprinuership da za'ay a gurin Sam baisan Yana ciki ba tunda kofar a rufe take ji yayi sosai Yana bada umarnin yanda abin ze kasance harda makudan kudin da za'a kashe gurin sawo kayan sana'ar da za'a koyar harda kudin da za'a participants din tunda program din harda matasan unguwa a cikinsa duk za'a Kuma bada kayan sana'ar da mutum ya koya kyauta, tun lokaci yayi masa alamar tambaya sai dai ba wata kafa daya Bari wadda za'a fashimci komai. Bai tabbatar da abinda yaji ba Saida akayi komai Kamar yanda ya bada umarnin, ga Kuma lokuta yawa sai yayi batan dabo ka nemeshi ka rasa Kuma har yanzu baisan takamaiamai Ina yake zuwa ba duk kuwa iya kwakwarsa. Jakar ya dauka yayi gaba Yana fadin Bari na Dan watsa ruwa na fito. Da ido suka bishi har ya shige corridor din daze kaishi bedroom dinsu,kowa Yana ayyana wani Abu a zuciyarsa. Ya dauki Kamar minti hamsin kafin ya fito cikin Riga da wando na shadda Fara tas, a gaggauce ya fito ganin lokacin sallar magriba ya kawo jiki. *** Da dare Zahra tana dakin Ammah suna Hira da Inna maimuna tana Kara nusar da ita yanayin rayuwa Sajida ta shigo da waya a kunnenta ta gaishe da innar ta Mikawa Zahra wayar tana fadin "Baffan Rimi ne yake son magana dake" Amsa tayi tare da sallama, cikin daki Inna ta nuna Mata da hannu ma'ana ta shiga ciki tayi wayar, Dan sajidar tana Mika Mata ta juya ta koma, haka Nan ta tashi duk da Bata San nufin innar na hanata waya a falon ba. Gaishe da Baffan tayi tunda Daman ya Santa tun suna makarantar kazaure sunje masa ita da Sajida lokacin da Zahrar ta zauna a kano gidansu sajidar sanda akayi musu hutun midtrem break maimakon taje Azare sai umman sajidar ta nemi Alfarmar Ammah ta barta tayi hutun a gurinta,to kafin su koma ne sukaje Rimin sumailar gurin kakan sajidar, tun lokacin ya baiwa Zahra magunguna sosai yace tayi amfani dasu har Sajida na mita ita Bai Bata irin na Zahra ba, a lokacin murmushinsu manya yayi Yana fadin "yanda aka saka rayuwarta a gaba ke ba Wanda ya damu da taki rayuwar ita akwai tarnaki Mai yawa a kanta Kuma Naga jikin nata ba wani abun azo a gani na tsarin jiki. Gaisuwar Baffa ya amsa Yana fadin "Ashe haka lamura sukayita faruwa ko Fadima? Dazu Babar taku tazo min da bayanin abinda ya ringa faruwa dake akan aurenki, yanzu haka tana Nan zata kwana saboda akwai abinda nasa ayi Miki gobe in sha Allah zatazo Miki dasu da yanda zakiyi amfani dasu in sha Allah ba abinda ze Kara faruwa dake, lallai akwai shedancin mutane akan lamarin Amma mu dauka Daman haka Allah yayi nufi, wanin Allah Bai Isa yayi maka komai ba face da izinin Ubangiji, ga Uwar taki ku gaisa". Ya mikawa Maman Sajida wayar. Bayan ta gaisheta ta Kara da yi Mata nasiha sosai itama, sannan ta fada mata gobe in Sha Allah daga Rimin Nan zasuyo ita da Babban danta Wanda some times shine direban ta idan zatayi doguwar tafiya, kafin sukayi sallama. Dakin Ammah Zahra ta shiga ta fada Mata yanda sukayi da kakan Sajida, godiya sosai Ammah ta ringa yi tana Kara jinjina kaunar da bayin Allah nan.suke yiwa Zahra dalilin 'yarsu gashi saboda matsalar Zahrar zata taso tazo har Azare. Washe gari tunda wuri Zahra da Sajida suka Gama gyaran dakin Ammah sukayi wanka sannan sukayi breakfast gurin karfe Sha daya Maman su Sajida da yayanta Ya Abba suka karaso murna gurin Sajida ba magana, dakin Ammah suka nufa da Maman Zahra tasonsu Fara shiga gurin Mama su gaisa Amma Sajida ta Hana tana fadin "A'a ki Bari mu shiga inda ya kamata idan min Gama abinda ya kawo ta sun gaisa da kowa so kike azo a zaune Mana a hana ruwa gudu". Tarba ta girma Ammah tayiwa Maman Sajida itama ba wata babba bace Dan Bata Kai sa'ar Ammah ba, an sauki Ya Abba a dakin da suke sauke bakinsu yayin da magaji ya shiga shidima dashi. Bayan Maman su sajidar ta Gama cin abubuwan da aka kawo Mata suka sake gaisawa dasu Ammah da Inna maimuna ta jajantawa Ammar abubuwan da suka ringa faruwa, ta Kuma Dora musu da bayanin da mahaifinta yayi Mata akan matsalar Zahrar inda ya bada tabbacin ko waye yake wannan shegantakar a kusa dasu yake sosai, Kuma dashi ake faduwa da tashi, kuma yace kada Wanda ya kawo wani Abu da sunan naci kona Sha yace a baiwa Zahra da sunan tsarin jiki ko na gyaran aure a barta taci sannan a kula da Koda abincin cikin gidan ne in dai ba ita Ammar ta dafa da hannunta ta Bata ba daga Nan har tabar gidan. Wata babbar leda ta dauko wadda sukazo da ita ta bude ta Ciro jarka da ruwa a cikin Mai kalar yellow na za'afaran ta dauko wani garin magani Mai laushi ta hadasu da jarkar ta mikawa Inna maimuna tana fadar. "Ga wanna ruwan addu'a ne da garin magarya zata dibi ruwan addu'ar ta zuba garin magaryar ta Sha ta shafe jikinta safe da yamma,wannan Kuma kafa da hannu kawai zata Riga turarawa sai Addu'oi da ya bada a Bata zata ringa karantawa safe da yamma". Godiya sosai su Ammah suka shiga jerawa Maman Sajida Kamar ba gobe har sai da ta ringa fadin "Haba Hajiya meye amfanin taren abinda ya shafi Zahra ai ya shafi sajida wallahi shekaranjiya data Kira ta fada min hankalina ba karamin tashi yayi ba wallahi na dauka abin ya kwaranye tunda an dauki dogon lokaci kafin a Kara maganar Auren". "Wallahi kuwa muma mun dauka na bayan da aka fasa ko matsalar namijin Aljani ne ya aureta Amma duk inda akaje da ita sai a ce ba wani iska a jikinta". Inna maimuna ta fada. Sun tattauna sosai da Maman Sajida Saida akayi sallar Azahar Sajida ta raka mamanta dakin Mama su gaisa, sun Sami kawar Mama Asabe sun hada Kai suna kus-kus bazaka taba cewa da mutane ba. Sun gaisa sajida ta fadawa Mama mamanta ce, Basu jima ba suka fito Mama ta biyosu har kofar part dinta Nan godiyar ziyarar. Sai kusan karfe uku su Maman Sajida suka juya Kano Sajida tace ita saita raka Zahra gidanta zata dawo. Tun da Mahmud ya Kira Zahra sau daya Bai sake kiranta ba, yau yaji ya kamata ya Kira yaji lafiyar ta ko banza fa yanzu tana karkashin ikonsa ne cinta da Shanta da duk lamuranta suna wuyans Kuma ai Bai kyauta ba gaskiya ace yayi burus da lamarin ta abun sai yayi Mata yawa. Sai gurin Tara na dare ya lalubo numbarta ya Kira, harta gama ringing ba'a dauka ba sai kawai ya share ya tura Mata text massage ya fada Mata Daman ya kirane yaji lafiyar ta. Tun bayan tafiyar Maman Sajida Ammah da Inna maimuna suka shiga hasashen abinda kakan Sajida ya fada na hasashen Mai yiwa Zahra bita da Killin nan duk iya nazarain su Basu gano ba sai suka.barwa Allah amma dai innar ta soke kwanan Zahra a can gurinsu tace su dawo dayan bedroom din Ammah suna wanna ita da Sajida da ita innar ya ishesu ita ko katifa sai a saka Mata a kasa ta kwanta. Hakan akayi su Zahrar suka tattaro suka duk wani Abu na amfaninsu suka dawo dakin. Kafin su kwanta Saida Inna maimuna ta saka Zahra tayi amfani da duk magungunan da Maman Sajida ta kawo Mata, wanna ne dalilin dayasa innar tace su dawo nan tunda komai na duniya Yana son sirri, duk da Hameeda ce kawai ke kwana a tare dasu Zahra Dan Salma tunda suka dawo ma Bata taba kwana a part din nasu ba. Tun Hameeda na jiransu Zahra su shigo har tayi barci. Saida Zahra ta Gama amfani da duk abubuwan da aka kawo Mata sannan ta dauko wayarta rabon data dauko ta tun bayan sallar Azahar data hau online ta duba sakonnin whatapps. Sajida da Inna maimuna Kuma sunta hirar duniya abunsu. Missed calls ta gani har hudu uku na mujiba ne sai Kuma wani daya number ce amma kallo daya tayi Mata ta gane ta waye, ji tayi gabanta ya fadi to neman me yake Mata da wanna tsohon Daren haka kawai ya dagula Mata sauran lissafinta. Fita tayi daga call history din sai Kuma taga envelope alama massage ya shigo budewa tayi sakonsa ta gani a hankali ta furta ta "Ya salam". Allah da gaske fa take jin wani irin lamari a tare da shi. Da safe ma innar ta saka Zahrar gaba Saida tayi duk abinda ya kamata kafin ta fice tabar dakin dan tun kafin ta Fara Sajida tayi waje ta Basu guri. Saida tayi wanka kafin ta fito yin break bayan sun gama ne Ammah tace Zahra taje Abbansu na kira, gyalen rigar ta yafa a kanta ta nufi gurin Abban, lokacin data shiga ya Gama break Shima, guri ta Sami ta zauna kusa da kujerar da yake Kai tana fadin "Abbana Ina kwana?" Jaridar dake hannunsa ya aje Yana fadin "lafiya kalau uwata, Ina fatan ba wata damuwa ko?" Kai ta gyada kafin tace "ba komai" "Masha Allah ya fada. Kafin yayi gyaran murya ya Fara fadin "Uwa inaga in sha Allahu jibi da yamma Zaki tafi gidanki Dan dazu ne malam Bukar ya roki wannan alfarmar saboda shi Mahmud din ne zeje wani taron da kunyar da suke aiki dashi suka shirya to Kuma yace baya son ya tafi Baki tare acan gidan ba kada abin ya Zama na magana ace ko ya gudu ne ya barki a nan, to Nima din na karbi nasa hanzarin tunda Masha Allah jikin naki yayi sauki sosai Kuma Baki bani kunya ba kin kwantar da hankalinki". "To Abba"abinda ta fada kenan tayi shiru, Mamace ta shigo dakin itama Tasha wanka sai baza kanshi take Kamar Kullum. Da barkwwnci ta shigo tana fadin "A'a bamu Gane ba, irin wannan kebewa tsakanin 'ya da uba mu ba'a neman ayi shawara damu". Ta fada tana fadada murmushinta. Gaisheta Zahra tayi kafin mamar ta gaisheta da Abban tunda ba itace da girki ba. Bayan sun gaisa ne yake fadawa mamar "Ba wani shawara muke ba wadda Bata shafeku ba Ina fada Mata ne jibi in Sha Allah zata tafi dakinta tinda Allah yasa ta warrare Kuma shi mijin nata ne zeyi tafiya shi yasa nake son ta tafi dakinta". Nisawa Mama tayi kafin tayi magana. "Kamar Yaya zeyi tafiya daga Kai masa yarinya basai ya tafi da ita ba salon ya cuci yar mutane ya lallaba ya budu ya barta tunda tsintacciyar mage ai Bata mage, gaskiya Abban Yara ka tsaya ka duba lamarin nan Mana kada fa azo ana Dana sani kaga masu iya magana na cewa keyace". Abban ne yace "ba abinda ze faru sai Alkhairi Amma Jibi da izinin Allah uwata zata tafi dakinta, tashi kije Uwata Allah yayi Miki Albarka yanda Kika yi min biyayya Ubangiji ya Baki 'ya 'yan da zasu yi Miki biyayya kema". A zuciyarta ta amsa da "Amin" Saida Abbai yaga ta fice gaba daya sannan ya dawo da dubansa gurin Mama yace "haba Rabi'a har yaushe Zaki dinga magama irin wannan a gaban kankanuwar yarinya Kamar Zahra ai Bai kamata ba ki duba kiga yanda aka dunga walagigi akan auren yarinyar nan a baya yanzu Kuma anyi aure Zaki ringa fito da maganganun da zasu iya sakata a wani Hali ai kwantar da hankali uwata take bukata ba irin haka ba, mu bita da addu'a in sha Allahu Alkhairi na hada Wanda a gaba duka sai sun gode min koda kuwa bana duniyar ne". Tunda Zahra ta shigo ta kwanta a kan sofa a nan falon Ammah na kallonta tasan kan zance dan tunda Abba ya dawo daga masallaci ya fada Mata, zancen da suke da Inna ma kenan ta shigo suka bar zancen. Da hantsin Ammah ta Kira Aunty Hasana ta fada mata. Zuwa Sha biyu tana gidan suna zaune a falon Ammah Mama ta shigo ita da kawarta ta amana Asabe wadda kwanan Nan ta mayar da gidan gurin zuwanta sabanin baya da sai a share watanni Bata zoba, Nan suka zauna akaci gaba da tattaunawa akan tarewar Zahra har Asabe ke fadin zata saka wata 'yar gusau da suke makwaftaka ta yiwa Zahra hadin kazar amare da daka shine nata Gudunmawar. Da yamma Aunty Hasana ta umarci Sajida da Hameeda da zilai Mai aiki suzo suje gidan Zahrar a gyara abinda ya kamata tunda jeren ya dan jima da yi. Sun fito zasu tafi ne Abdul Hakeem ya tsayar da Auntyn Yana fadin "sai Ina Kuma Aunty mu?" "Gidan Zahra zamuje a Dan Kara gyarawa jibi Abba yace za'a kaita kaga kuwa ai dole a shiga a duba ayi abinda ya kamata". Komai tsab suka sameshi da gani ana gyarawa Kullum dan har wani hadaddan kamshin freshner ke tashi a falon haka bedroom din Shima komai neat yake a toilet ne abin ya bawa Aunty Hasana mamaki an zuba kayan wanka masu azabar tsaba Bata Kara tsinkewa da ta janyo locker ta jikin mirror taga wasu designers din turaruka na Mata Kuma da yawa na kamfanin Al -haramain ne harda irin Wanda Zahra take amfani dasu. Ita dai Hameeda Yar kauye ta Zama a gidan Dan ko a mafarki Bata taba kawo Wanda aka aurawa Zahra, ze Kama hayar gida irin wannan aljannar duniya haka ba. A kitchen ma Nan Hameeda da zulai suka lalace komai na gurin saiya burge mutum, Nan ma Saida Auntyn taga wani fregde ash colour a cikin Dan ack din jikin kitchen din irin Mai kofa Kamar ta wadroof ko ba'a fada ba kasan kudi sunyi kuka a gurin. Burner Auntyn tasa aka jona aka zuba turarikan wuta Wanda aka hadowa Zahra daga Saudi Arabia tun wancen lokacin tunda basa komai saima Kara kamshi. Basu baro gidan ba sai kusan magariba. Aunty Hasana taso ta wuce da Zahra gidanta amman Ammah tace A'a ba inda zata so suke ace Mata tsohuwar banza idan so suke su tafi to ita zahrar ta Kira ta fadawa mijinta idan ya amince ita nata Mai sauki ne ita kuma Zahra tace lahlah a barshi kawai. Wajen goma saura aunty Hasana ta dauki yaranta suka wuce gida. Da safe Saiga Asabe da dahuwar kazar amare da jarkar zumar Mata da ta tsimi tayiwa gidan tsinke, part din Ammah ta shigo direct, bayan sun gaisa ne ta mikiwa Ammah babbar ledar data zubo kayan tana fadin "Ina Amarya tazo gashi na cika Alkawari tazo ta cinye ta bani kashin tace a koma Mata dashi zata hada Mata wani Abu dashi. Inna maimuna ce tace "ai kuwa yanzu taci abinci ta shga daki saidai a aje zuwa anjima sai taci ko gida ne sai a aika Miki da Qashin, mun gode kwarai madallah Allah yabar zaman tare". Asaben ta amsa da "Amin ai bama sai an tashi mutum ya kaiba Nima saina jira taci din ko Nan da yamma ne" ta fada tana mikewa tayi musu sallama ta nufi dakin Mama. Bayan fitarta ne Ammah ta dubi Inna maimuna tana fadin "nifa jikina Bai bani ba akan taci wanna abun Dan ni tunda ta fada jiya naji abin Bai kwanta min ba,mutuniyar da gaisawa ma sai ta kure akeyi da ita Amma fa ki duba sai wani rawar jiki take akan abinda Bai shafe ta ba ko alama, Kuma kar nice wani abun arziku sukeyi da zahrar Dan ko gaisawa saita kure, Amman ki duba ki gani yanzu sai haba haba take da Zahra. Dakin Ammah aka shiga da kayan ammar tace zata cire tsokar tabar musu kashin, hakan ne ya kasance tayi komai ta baiwa auta ya kaiwa Asaben dakin Mamar. Saida Asaben ta tabbatar auta ya fito ta kwashe da dariya tana fadin "wallahi Maman yara kinsan ta kan mugumta, yarinya har yarinya amma ta Kare a auren marar asali Wanda ko danginsa ba'a sani ba" Kwafa Maman tayi "barni kawai Asabe wallahi tun lokacin da aka dauko yarinyar nan hankalina ya kasa kwanciya, saboda babu ta inda Allah ya rageta duk abinda ake so jikin 'ya mace to Allah yayi Mata ga uwa uba yanda mazan zamanin nan suka jarabtu da son Mata irinta nasan ba karamin mutum ne ze dauke taba Ina zaune sai dai na Zama 'yar kallo ga nawa 'ya'yan a gabana, wallahi baze yuwu ba ai hankalina Bai Kara tashi ba Saida na raka Aunty Ladi gurin wani Mutum a can jos nayi Masa maganar Asma'u to cikin binciken ne maganar yarinyar ya Fado yake fada min na kyale maganar Asma'u don ba yanda zanyi da ita jikinta a shirye yake haka Shima Alhajin ba abinda zeyi tasirin da ze rabashi da ita, Amma ga wata yarinya Nan duk gidan ba 'yar da zata wuceta a sa'ar rayuwa a gurin aure Dan mijin da zata aura ba karamin mutum bane Kuma dai..... Sai kawai bawan Allahn Nan yayi shiru da bakinsa nayi nacin duniyar nan Amman yaki karasa mana zance, haka muka tasho Aunty Ladi nata zugani kada na kuskura na Bari ta auri Mai maiko duk yanda zanyi nayi Naga hakan Bata faru ba. Nayi ta fama duk Wanda zezo gidan Nan gurin yarinyar nan zezo duk kuwa da Fadi tashin da nake akan su Salma amman a banza, maganar dai daya ce Zahra, ni Kuma nayi Alkawarin badai Zahra tayi aure ta barmin Yara a gida ba,Kuma badai ta auri Mai rufin asiri ba, gashi kuwa ta Kare a Wanda ko asalin kirki bashi dashi Abu daya ya tsaya min a Rai yanda Naga gidan da zata zauna da abin yaso razani sosai Dan ba haka na zata ba, amman duk da hakan ma yayi tunda ai gidan ma Malaminsa ne ya bashi aro su zauna, Kinga kuwa karshe sai dai a Kare a yawon haya cikin Yama yamar matan alarammomi, Kuma wannan kayan da ake qafafar an saka a gidan karshen wasu kayan saidai a sayar Dan Babu abinda za'aci dasu Dan an sawo da zimmar su tafi Abuja sai gasu sun Kare a gidan Alaramma". Ta fada cikin izgilanci. ** Duk yanda Zahra taso ta kwantar da hankalinta abin ya faskara dan da gaske zulumi takeyi na yanda zata fuskanci wannan sauyin da yazo Mata a bazata Wanda Bata tab'a tunanin hakan ba ko cikin mafarki, lallai tayi zaton daga kan Mushahu komai ya kwaranye Amma sai wata matsalar ta taso wadda tafi ta baya. A kwance ta wuni duk ta tsangwami kanta Sajida sai tausarta take duk da itama tata zuciyar a kusa take Dan da gaske tana tausayin zahrar ba kadan ba. Gurin karfe biyu ne sukaji alamar Kamar anyi Baki a gidan da alama ma da dan damarsu. Sajida ce ta fito ta gaishesu zata koma cikin ne Ammah tace taje ta Kira Mama tace tazo su gaisa da Baki Iyayen Musbahu ne daga kano. Ta fita tana mamakin to meya kawo su Kuma. Tare suka shigo da mamar Dan sajidar na fada Mata ta nufo dakin cikin rawar jiki. Ciki Sajida ta wuce yayin da mamar ta zauna tana gaishe da bakin nasu Kafin Inna maimuna ta Fara Mata bayanin Maman Musbahu ce tazo da 'yan uwanta ta bada hakurin abinda ya faru Wanda ita kanta Bata San yanda akayi ba sai daga baya ake fada Mata shine tazo taji ko da yanda za'ayi a gyara matsalar tunda ta dawo hayyacinta take cikin damuwa domin kwata kwata Musbahun baya cikin nutsuwarsa tun bayan samun labarin an Aurar da zahrar, ganin lamarin nasa ba sauki ne yasa suka nufo nan Ashe har da yaron sukazo sun jima a gurin Alhaji ma kafin su shigo nan din, hakuri kawai ya basu akan aikin Gama ya Gama tunda yanzu matar wani ce ita. Kallonsu Mama ta karayi tana tambayar "Ina mamar tasa take" Hajiya Nafisa kanwarta ita ta nuna Maman Musbahun tana fadin "gata nan" "Ayya Allah sarki Hajiya sai hakuri Allah Bai nufa matarsa bace ba sai dai yazo ya duba wata tunda da sauran yaran a gidan". Mama ta fada tana kafe Hajiyar da ido. "Kayya a yanzu dai bana tunanin haka zata yuwu sai ko a gaba tunda ban taba ganin abinda Musbahu ya kwallafawa Rai ba Kamar auren yarinyar nan tunda kuwa ya rasa ta bansan Kuma lokacin da ze Kara maganar wani auren ba". Sun Dan Jima kafin Ammah ta tashi ta shiga gurin su zahra tace ta fito su gaisa da Baki zasu tafi. Jiki ba kwari ta nufo kofa doguwa rigace a jikinta kirar Bahrain Mai duwatsu har kasa blue black gyqlenta kwai ta Dora a kanta Dan Sam Zahra Bata fiye son saka hula ba a kanta Dan Sam santsin gashinta baya Bari hular ta zauna ta dunga zamewa kenan. Cikin takunta na nutsuwa ta shigo falon hade da sallama Kanta na kallon kasa ta karaso cikin nutsuwa ta zauna gefen Ammah a kasa kan carpet, tunda ta shigo suka bita da idanun kowa da abinda yake ayyanawa a zuciyarsa. "Masha Allah! tubarakallah 'yata matso kusa dani dole my son yayi kamar ya zauce da labarin rasaki ya riskeshi" abinda Aunty Nafisa ta fada kenan tana nunawa Zahra kusa da ida, jiki ba kwari ta karaso ta zauna tana gaishesu. Suka amsa jiki a sanyaye su kansu sun San dansu yayi wani babban rashin da maida shi sai nufin Allah, tunda Daman shiya hada shi da Zahrar kuma shiya raba lokacin daya so. Nan sukayi sallama suka fita cikin matukar jimami Dan da gaske sunyi rashin sirika. A daki Zahra kwanciya bayi ta rufe fuskarta da hannu biyu Batasan lokacin da hawaye ya zubo Mata ba, Wai shike nan komai ya Zama past tsakaninta da Musbahu duniya ba tabbas. sajida na kallonta Bata hanata ba Dan itama Saida ta matse, lokacin zahra na falo Mushahun ya Kira wayar ta, sajidar ta dauka yanda taji maganarsa ko rantsuwa tayi bazatayi kaffara ba kuka yake shima da idanunsa Dan abinda ya fada kawai ya karya Mata zuciya, kalamai ne na bankwana ga masoyi da da given off akan Abu, da kyar ta iya fada Masa ba zahra bace itace magiya yayi Mata dan Allah ta fito Masa da zahra yayi Mata sallamar karshe Amma hakuri kawai ta bashi tunda yanzu Zahra matar aure ce bashi da hurumin yin magana da ita. Sun Dade a haka kowa da abinda yake sakawa a zuciyarsa nkafin su jiyo maganar Magaji Yana fadin "Ammah ga Ya Mushahu zaku gaisa yazu tafi ne". Su biyu suka shigo suka gaishe dasu Ammah a nan Inna maimuna ke fadin "kayi hakuri da hukuncin Allah kaji kada kayi fushi da mahaifiyar ka itama bayin kanta bane duk uwa bataqi ace danta yafi kowa sa'ar abokiyar Zama ba, irin wannan matsalar ta Jima tana bibiyar yarinyar Nan to munyi zaton daga kanka abun ya Kare sai Kuma ya canza salo akan mahaifiyar ka, kayi hakuri ka fawwalawa Allah komai shi ze baka wadda tafi Zahra daman Allah hukunta kai ba mijinta bane ayi hakuri". Kansa Yana kasa tunda ta Fara maganar wani Abu ya tsaya masa a makogwaro yaji Sam ya kasa magana sai Aliyu ne ya amasa da "ba komai Mama haka Allah ya nufa, Allah ya Basu zaman lafiya mu zamu koma". "To Allah ya tsare ya baka mace ta gari wadda zata maye maka gurbin Zahara'u" Inna ta fada ita kuwa Ammah kasa magana tayi dan da gaske yaran tausayi suke Bata sun kwallafa Rai da juna Amma akayi musu karan tsaye, a zuciyarta ta ayyana "Allah ka biwa yaran Nan hakkinsu duk Mai hannu a cikin Bata lamarin Nan kayi Mana sakayya da gaggawa Dan isar Annabin Rahama Muhammad s.a.w.w." Ta window zahra ta leka lokacin da suka fito daga falon kamar ance ya juyo sai ganin zahrar yayi tana kallonsa da sauri ta juya ta rufe fuskarta da hannu ta saki wani marayan kuka ta zube a gado. Su Kuma suka fita zuciyarsa Kamar zata Kama wuta dan ganinta ba karamin fami ya zamar Masa ba, har ji yayi Yana wani layi Kamar ze fadi. Magaji ne ya shigo falon Yana fadin "Sun tafi, wallahi Ammah naji tausayin Ya Musbahu sosai kinsan har gurin Baba malam yaje Amma magana daya dai kowa yake fada masa yayi hakuri, bayan mun fito ne yace na nuna Masa mijin Aunty zahrar na fada Masa ai shine suka Fara gaisawa dashi bayan sun gaisa da malam, shiru yayi sai kawai Naga ya dafe kansa Yana girgizawa, yace na hakura da zahra nasan wannan baze taba sakin zahra ba. wallahi Ammah sai Naga yana goge hawaye gaskiya Allah saiya saka musu wannan ai zalunci ne Kullum idan Aunty zahra ta samu miji sai an samu matsala". Ya fada Yana Jan tsakin takaicin. "To magaji babu yanda za'ayi haka Allah ya hukunta sai hakuri". Bayan tafiyarsu da Kamar awa daya Abdul Hakeem ya shigo ya fadawa Ammah tazo Abba Yana kiranta. A bedroom dinsa ta sameshi Yana tsaye ya goya hannunsa a baya Yana Dan Kai kawo a tsakar dakin. Sallam tayi Masa ya amsa sannan ya sauke hannunsa ya nufi gefen gadon inda Ammah ta zauna tana tambayar "Lafiya kuwa Abba meya faru Naganka a haka?" Ajiyar zuciya ya sauke Yana fadin. "Da matsala gaskiya yaron nan ne yazo a rikice yana kuka Kamar yaro karami da kyar muka lallashe shi nida Abdul Hakeem ga mahaifiyarsa da 'yan uwanta kingansu dai nasan mazan ne suka ce ba ruwansu shine ita da kanta ta taso tazo wallahi hawaye bibiyu ta rinka yi min akan na rufa Mata asiri na warware wancan auren a maida kan Musbahu abin har abin tausayin wallahi, shi yasa na turosu cikin Dan ku Basu hakuri tunda wancen zance ya wuce Kuma ji nayi da nauyi na Kira malam wallahi tunda ganin Mahmud nake Kamar Dan cikinsa Kinga na Kira shi akan maganar ai Bai kyautu ba, to bayan sun tafi ne Abdul Hakeem ya Kira Hassan ya fada masa shine ya kirani Yana min magiyar Dan Allah a rakata dakinta yau basai gobe ba da tun farko ma ankaita da hakan Bata faru ba yasan wasu ne daga nan zasu Gaya Masa tunda Yana da mutane sosai suce ai tana gida ma yayi bata tare ba suyi tunanin ko Babu auren ne, Dan haka Nima nayi na'am da maganar tasa, kuje kuyi duk abinda ya kamata da magariba zan mikata dakinta da kaina in Sha Allah, na Kira malam ma na fada masa." "To hakan yayi duk abinda ka yanke dai dai ne Allah ya nuna Mana lokacin". "Amin ya amsa".... ✨✨ AUREN HUCE HAUSHI ✨✨ ❤️❤️ ❤️❤️ 💋💋 💋💋 MAMAN FATIMAH. PAGE SEVENTEEN (17) _________ Karfe biyar mai kyau motar da Alhaji Jafar ya tuko da kansa daga shi sai Zahra a ciki daga bayansa Kuma Abdul Hakeem ne a wata motar ya biyo Abban nasu bisa umarninsa,suka dira kofar gate din gidan Zahra,sau biyu Abban yayi horn Mai gadin ya leko da yaga Alhaji ne da kansa tunda daman ya San Alhajin farin sani yayi sauri ya bude kofar suka shigo gaba daya, da sauri Mai gadin ya karaso Yana budewa Alhajin kofa Yana gaishe shi yayin da Abdul Hakeem ya budewa Zahra ta fito suka zagaya Gurin da Abban yake, Abdul Hakeem suka gaisa da Mai gadin sannan Abban ya Kama hannun Zahrar ya nufi kofar main falon da ita, tasha farar laffaya Mai adon kananan flowers pink, jikinta kamar an Mata barin turare sai tashin kamshi take Mai Dadi. A bakin kofa suka Hadu da Mahmud din ya nufo kofar da sauri Dan Yana bedroom dinsa yaji shigowarsu tun bayan anyi la'asar Baba malam yace Alhajin yace ya same shi a can gidansa da yamma za'a kawo Masa iyalinsa. Matsawa Mahmud din yayi daga bakin kofar Yana yiwa Abban sannu da zuwa sannan ya mikawa Abdul Hakeem hannu suka gaisa, kan kujera Abban ya zaunar da Zahra sannan ya umarci Mahmud daya zauna kusa da ita shi Kuma ya zauna a kujerar dake kallonsu, Abdul Hakeem Shima ya zauna, sai falon ya dauki shiru, gyaran murya Abban yayi kafin yace "Abdul Hakeem yi Mana addu'a' bayan yayi doguwar addu'a sun shafa Abban yace "To Mahmud ga matarka nan na kawo maka bani na baka ita ba Allah ne ya baka ni nawa idawa ce, gata Nan amanace a gurinka kada ka zalunce ta duk inda yanayin rayuwa ya kaiku na baka ita ne saboda na yaba da nagartarka na Dade Ina monitoring dinka ban tabaji ko ganin abun ashsha ba a tare da kai, kullum addu'ata Allah ya bani ikon sauke nauyin marainiyar Allah dake hannuna, kuma Alhamdulillahi na sauke gata nan marainiya ce Bata da uwa Bata da uba ba wa ba kani ita kenan iyayenta duka suka rasu suka barta, kada ka zalunce ta Dan girman Allah ka tausaya Mata saboda Mai rauni ce, ka zamar Mata uwa uba abokin Shawara kuyi dariya tare kuyi kuka tare ka jibinci lamarinta gwargwadon iyawarka. Ina Kuma Kara gode maka bisa share min hawayena da kayi baka watsamin kasa a ido ba lokacin Dana baka aurenta, na gode kwarai Allah ya saka maka da Alkhairi ya yaye maka damuwarka ya kawo maka mafita a bisa lamuranka". Suka amsa da "Amin" Sannan yaci gaba da fadin "ke Kuma Uwata ga mijinki nan kiyi Masa biyayya abisa abinda Bai sabawa Allah ba, ki girmamawa shi ki kiyaye bacin ransa ki kiyayie mutuncinsa da rike Masa sirrinsa kindaraja mas iyayensa da 'yan uwansa lokacin da Allah ya hukunta ku hadu dasu,nkiji tsoron Allah a cikin zamanta kewarku ki saka hannu ki Barbi duk abinda ya biyo bayan aurenki dashi Mai Dadi ko sabanin hakan. Dan Allah ki kwantar da hankalinki kiyi hakuri da abinda Allah ya hukunta a kanki komai Kika gani rubutacce ne daga Allah sai dai mu 'yan adam mu karasa shi, Amma tun ran gini tun ran Zane dama haka kaddarar take, ko shi mijin naki idan yayi nazari zega wata kila wannan kaddarar auren ce ta rabo shi da asalin inda yake, to Dan haka kowa ya rike tasa kaddarar wata Rana sai labari komai na duniya Yana da iyaka ikon Allah ne kawai bashi da karshe, Allah yayi muku Albarka ya kauda fitina a tsakaninku ya tabbatar da Alkhairi a cikin rayuwar aurenku, Mahmud sai anyi hakuri da Mata su masu rauni ne kwarai da gaske". Tunda Abba ya Fara magana yaji kamar ya dauko wani gaigimemen dutse ya Dora Masa aka. Cikin ladabin da baisan Yana dashi ba ya furta "in Sha Allah Abba ba wata damuwa Kuma amana na karba na rike Allah ya bani ikon saukewa nike da godiya Allah ya saka da Alkhairi ya Kara Nissan kwanaki masu Albarka" "To Masha Allah, Abdul kayi Mana addu'a mu tafi kada almuru tayi Mana a nan, Uwata ki daina kukan Nan haka bana sonsa kiyi hakuri kowa da haka ya girma Allah yayi Miki Albarka, ga makullin motarki wadda mukazo da ita takice na sai miki, kudin dayar ta wajen Abbie suna gurin Alhaji muttaka tunda aka sayar da ita nace ya juya Miki kudin zuwa lokacin da za'a bukaci wata motar Dan haka in Sha Allah cikin sati Mai zuwa za'a kawo Miki dayar ma". Suka tashi suka fita Mahmud yayi musu rakiya har gurin mota Saida suka tafi sannan ya dawo ciki, a inda ya bar zahrar anan ya sameta ta kwantar da kanta a kan cinyoyinta tana kuka Mai tsuma zuciya a hankali ya zauna kusa da ita yasa hannu ya dago kanta daga jikin cinyoyinta idanunta a rufe sai tsiyayara da ruwan hawaye suke. Ba zato ba tsammani kawai taji ya sakata a girjinsa ya kwantar da kanta ya saka hankici Yana share Mata hawaye, daya hannun Kuma Yana tapping din bayanta kamar yanda ake yiwa yaro idan ana so yayi shiru Yana kuka, jikinta gaba daya ya dauki rawa ta taso da niyyar zare jikinta Dan wani Abu takeji duk ilahirin jikinta Amma Dan bawan Allan nan yayi kememe yaki sakinta ba arziki ta hadiye kukanta, sai sauke ajiyar zuciya kawai ba kakkautawa saida ya tabbatar ta Samu dan nutsuwa sannan ya saketa Yana fadin " sorry Baby ki daina kuka bana son kuka Sam koda kuwa na karamin yaro ne". Hannunta ya Kama ya mikar da ita ya nufi daya daga cikin bedrooms dinta guda biyu da suke mallakinta, Saida ya zaunar da ita a gefen makeken gadon sannan ya juya ya nufi kofa Yana fadin " it's time for prayer" Ya fice Yana ja mata kofa. Sai ta dauki kusan minti biyar kafin ta Samu kuzarin warware Laffayar dake nannade a jikinta, doguwar rigar material ce a jikinta anyi Mata dinkin fitted gown tayi Mata kyau sosai kofar data gani ta nufa tasan toilet ne, lokacin data shiga abin ya girgizata irin kayan amfanin data gani a ciki ita ba bakuwar abin bace tasan ba kananan kudin aka narkar ba a cikinsa, abin ya Bata mamaki sosai sai dai wa zata tambaya? ta Jima a ciki kafin ta dauro alwala ta dawo dakin. Ido ta ringa wurgawa ko zata ga sallaya tunda ita dai bakuwa ce a dakin can gefen sofa taga wani stool kamar coffee table da sallayun akai ta shimfida ta Fara sallah. Tana cikin sallah ne taji kamar karar door bell kamar sau biyu, Saida ta idar ta tashi ta fito har lokacin tana share hawaye jefi- jefi, gurin kofar ta karasa ta bude Sajida da Hameeda da Mujiba ta gani ai batasa lokacin data fada jikin Sajida ba tana dakin kuka Mai tsuma zuciya. Ciki suka shigo Sajida na fadin "haba bestie wallahi Dana San har yanzu baki daina kukan Nan ba da bazamu biyo bayanki ba, haba Ashe bazaki karbi kaddara yanda tazo Miki ba? ki Kuma godewa Allah a kowane Hali Kika Samu kanki, bake Kika halicci kanki ba ballantana ki tsarawa kanki yanda Zaki rayu, kin taho kina kuka duk kin dagawa Ammah hankali itama, kin kyau kenan? haba kiyi hakuri Dan Allah ki share hawayenki wallahi nasan yanzu zuciyar masu binki da mugun nufi tana can kamar zata fashe Dan ba haka suka soba duk da bansa daga Ina matsalarki take ba, ai kodan makiya kin kwantar da hankalinki ki rungumi mijinki ki ba mara d'a kunya, Amma kin tsaya kina wani Abu kamar wata karamar yarinya" Tayi tsaki tana kallon zahrar da tayi kozai kozai ido ya kode Mata abinka da farin mutum. Suma su Hameedar ban baki suka dunga yi Mata, da kyar ta hadiye kukan ta kallesu tana fadin "wallahi bazaku Gane bane ni kadai nasan me nakeji, komai ya kwance min Sam duniyar bata mun dadi". "Hakurin dai zakiyi ki Kuma yawaita addu'a in sha Allah komai ze wuce kamar ba'ayi ba, muda muke son next year by now mu dawo suna". Sajida ta fada tana murmushi. Wani kallo zahrar tayi Mata ta juya kanta gefe tana fadar "Allah ya kiyaye min wata haihuwa can". Mujiba ce ta kwashe da dariya tana fadar "A'a Banda cika Baki dai 'yan Mata Nan da labari yasha banban zamu tsinceki kina faman 'yan amaye amaye, lokacin ne Zaki gane Baki da wayo ko ba wata haihuwa can ba?". Zumburo Baki tayi tana fadin "sai kiyi Kuma haka kawai Zaki jaza min, wani ciki ko dadin fada ma Babu". Saima zahrar ta zame ta kwanta, tana jinsu suna ta faman zolayar ta har aka Kira sallar insha'i a Nan sukayi sallah kafin su shiga Kara gyara Mata Fallon da Kara masa freshner da turaren wuta Hameeda ta Kara karfin A C a falon ta gyara cutains din, bedroom din data fito suka shiga Mujiba bakinta ya kasa shiru tunda dai suka Samu zahrar ta daina 'yan koke koken sai ta balle da santin gidan Dan bayan sun idar da sallar ba inda Bata shiga ba ta leka can ta shiga can bedroom din Mahmud ne kawai Bata shiga ba tunda a rufe yake, fada take "wallahi zahra ki Kara godewa Allah, irin wannan haduwa haka wallahi ko makiyi Saida yaki fada Amma dai duk wani gata kin same shi sai dai fatan zaman lafiya kawai". Ita dai Zahra ba baka sai kunne.Dan ita kadai tasan abinda ke Kai komo a zuciyar ta, su inda suka dosa daban ita inda ta dosa daban, ko tayi musu bayani ba ganewa zasuyi ba, domin su duka ba wadda ta tab'a shiga irin gararin data shiga, rayuwa Rumi rumi saika Gama sakankancewa da mutum Rana tsaka Abu ya lalace, uwa uba ganin da tayiwa Musbahu ba karamin famu yayi Mata ba, saboda da ta cire shi daga ranta kwata kwata ta hakura, Amma tana ganinsa komai ya rikice Mata da tana zargin kamar da niyya mamansa tayi haka saboda ya taba fada mata Maman nasa taso ya auri 'yar Yayarta shi Kuma ya ringa sharewa ana haka ne Allah ya had'a shi da zahrar abinda ya kawo karshen wancan dambarwar kenan. Amman tasowar mamansa da 'yan uwanta dashi kanshi takanas ta kano har Azaren don bada hakuri da neman gyara idan lamarin Mai gyaruwa ne, sosai abin ya tashi hankalinta, wata sabuwar soyayyar sa ce ta sake bijiro Mata idan tana tuna yanda yaci buri a irin wannan ranar da za'a kawo Masa ita a matsayin matarsa ta sunna halalinsa, irin abinda yake fadin ya tanadar Mata ita a wancen lokacin idan Yana fada kamar zata nitse kasa dan kunya Amma shi ko a jikinsa. Wasu sabbin hawayene suka zubo Mata masu zafi tana ayyana shike nan komai ta Zama tarihi, ga inda kaddara ta kawo ta gurin da ba'asan darajarta ba ko alama sai aukin taba Mata jiki da yake Wanda ta fashimci hakan tun haduwarsu ta farko, ba kunya ya wani saka hannu ya rungumota Wama ya sani ko Dan duniya ne aka hadata dashi, tunda ance ba Wanda yasan asalin sa kuma tasan yanda yake din nan ko bashi da sisi mata zasu ringa kawo Masa rida tunda sun ganshi smart dashi. Wani tsaki tayi tana ayyana to Ina ruwanki da wani smartness dinsa. Mahmud Bai dawo gidan ba sai bayan sallar insha'i ganin takalma yasan akwai baki cikin gidan baya raba daya biyu 'yan uwanta ne ko kawaye, dakinsa ya wuce yayi wanka ya canza kaya ya fito falo, bai shiga dakinta ba daga inda yake yana jiyo mganganun bak'in, ita dai baiji tata maganarta ba Sam Zama yayi yana daddana wayar hannunsa. Acan Kuma dakin Zahra Ya Abdul Hakeem ne ya Kira wayar Sajida Yana fada Mata su fito su tafi ya dawo daman lokacin daya basu kenan bayan sallar insha'i lokacin daya kawo su. Sun fito falone suna zolayar Zahra Basu kula da mutum ba sai da suka sauko daga steps din da ze sada ka da corridor din bedrooms din suka ganshi a zaune Yana ta faman Danna waya, kallo daya Zahra tayi Masa ta kauda Kai haka kawai taji gabanta ya fadi, ta rasa wace irin masiface wannan. Kansa ya dago yana amsa gaisuwar su Sajidar Yana fadin "har zaku koma ne?". Hameeda ce tayi farat tace "To ba dole mu tafi ba yallabai tunda angon yaki zuwa ya sayi bakin amaryarsa ba Yana ganin Mai araha ce bai Sha wahalar komai ba aka bashi ita". Ba Zahra da aka ciwa fuska a fakaice ba hatta Sajida da Mujiba Saida sukaji kamar kasa ta nutsa dasu a gurin Dan kunya, gaba daya suka zubawa Hameeda ido har shi uban gayyar, wani abune Wanda Zahra Bata taba tunanin Hameeda zatayi Mata ba, dan wannan cin fuska ne qarara bako kawaici a cikin maganar ko kad'an. Zahra kasa gaba ko baya tayi ta tsaya a gurin kawai, su sajida ma rasa ta cewa sukayi shi kuwa uban gayyar wayar dake hannunsa ya aje Yana kallon Hameeda direct kafin yace " waya fada Miki Mai araha ce bakiji sunanta ba? Zahra fa kinsa ma'anar sunan kuwa? tauraruwa fa a cikin taurari a gurinki take Mai araha Amma ni a gurina tafi zinari daraja, bari na baku indai abin sayen Baki ne in dai shi ne abinda ke shaida Kima da darajar mace a irin wannan ranar gurin kawayenta, ina zuwa". Ya fada Yana mikiwa ya nufi hanyar bedrooms dinsu, tunda ya wuce zahra ta juya da sauri ta nufi daki Bata yi musu ko sallama ba. Bai jima da shiga ba ya fito da wata katuwar leda da Kuma envelope guda uku a hannunsa. Yana zuwa directly Hameeda ya nufa ya Mika Mata ledar da envelope daya sannan ya baiwa Sajida da Mujiba Suma dai dai Yana fadar "ga kayan sayen bakin Nan a cikin wannan envelope din Kuma kunsha ruwa a hanya". Ba kunya Hameeda tace yanzu naji magana ai shi tuwon girma miyarsa Nama mun gode". Taja katuwar ledar tayi gaba abinta mujiba ma tabi bayanta har suka fita Sajida Bata motsa ba ita kollon ikon Allah take akan Mahmud Wai wannan shine Almajirin da ake ta yayatawa a aurawa Zahra har Hajiya Mama na yiwa Abba magiyar kada ya Fara wanna danyan aikin tab wallahi da sake ita tafa abinda ta gani ga tare dashi ai da hasashe ne take yanzu be taga zahiri. Ganin sun fita yasa sajidar aje Masa envelope dinsa a gefen shi tana fadin "kabar abinka na gode, ni fatana ka rike min bestie da mutunci da amana yafi ka bani duk abinda ka mallaka, bansan Kai ko waye ba Amma jikina Yana bani kana boye wani Abu tun lokacin Danazo gidan nan da Kuma irin kayan danaga an kawowa bestie nasan Kai ba kaskantanccen mutum bane, Ina hadaka da girman Allah kada ka bautulcewa Iyayenta da suka baka ita kaji tausayinta marainiya ce, Dan Allah nasan duk inda ka fito ba karamin guri bane ka Zama garkuwarta ka zamar Mata bangon da zata jingina taji dadi duk rintsi. Dan Allah ka Bata kulawa Zahra 'yar gata ce kaddara ce ta zaunar da ita a kasar nan da Kuma kawaicin kakanninta suka hakura suka barwa Ammah ita, Dan Allah ga amana Nima na baka kamar yanda iyayenta suka baka kaji tsoron Allah a cikin zamantakewar ka da ita na San Nan gaba zaka samu zabinka ko Kuma tuntuni kana dashi Dan Allah kada ka wulakanta ta.. na rokeka ka Zama adalin shugaba a gurinta idan kaji yanda rayuwa ta dunga jujjuyata zaka tausaya Mata matuka, Dan Allah badan niba...." Da tayi gaba ta nufi kofa Bata taji me ze fada ba domin hawayene suka ciko Mata idonta idan tace zataci gaba da magana kuka zata fasa masa ne. A bakin kofa sukayi kicibus da Mujiba wadda ta dawo kiranta ganin shirun ya yi yawa. ✨✨ ✨✨ AUREN HUCE HAUSHI ✨✨ ✨✨ 💎PAGE EIGHTEEN💎 STORY AND WRITTEN BY MAMAN FATIMAH. _________ Bayan wucewar Sajida Mahmud ya Dade Bai tashi ba, kwarai yarinyar ta burge shi matuka, da gaske take son Zahra domin furucin da yarinyar can tayi yayi touching dinta sosai, lallai ya tabbatar son da take yiwa Zahra bana Wasa bane shi tun lokacin da Magaji ya fada masa ta baro syprus Dan kawai ta halarci bikin zahrar ya jinjina Mata duk da suna hutu Amma yasan irin wadannan daliban ba kowane hutu suke zuwa gida ba sai dai idan iyayen sun sunci sun tada Kai. Envelope din data aje masa ya kalla yayi wani killer smile ya zurata a aljihun Wando Yana Kara wani murmushin Wanda shi kadai ya barwa kansa sani. Yaso ya shiga dakinta sai ya share kawai Dan yasa baya raba daya biyu kuka take Dan da gaske koshi baiji dadin furucin da akayi Mata ba Kai tsaye bako rusunawa a ciki. Lokacin da Abdul Hakeem ya Parker motar a parking lot na gidan Sajida ce ta farkon ficewa daga motar zuciyar ta na Mata wani zafi Dan da gaske idan ta tsaya zata shatawa Hameeda rashin mutunci ne na karshe Wanda zata Dade Bata manta ba, dan da gaske an shirya ne kawai dan a tozarta Zahra a gabanta mijinta, shi yasa kenan lokacin da zasu ltafi ta shiga part din Mama Kiran Hameedar akan ta fito suje, taji Salma na fadin saura Kuma ki kasa fada ki dawo Mama ta tumurmushi banza, ita Sam Bata kawo komai ba kawai dai ta dauka wani abune can tsakaninsu saida hakan ta faru ta Gane me ake nufi da waceccen maganar. Tana jin Mujiba na kwala mata Kira lokacin data nufi karamin gate wanda ze sada ta da cikin gidan, batabi ta Kanta ba tayi wucewarta ciki ta kyalesu. Koda ta shigo part din Ammah directly bedroom din da suka kwana ta wuce tana yiwa su Aunty Hasana sannu har ta shiga ta fito tana fadin "Aunty Dan Allah idan su Hameeda sun shigo kice su raba kayan su biyu kwai Banda ni". Ta koma da sauri Dan tana jiyo maganar su a kusa alamar Nan suka nufo. Tun shigar Zahra bedroom din Nan ta kwanta rub da ciki take risgar kuka Kamar ba gobe, Hameeda ta Bata mamaki Bata taba zaton irin wannan ranar ba a tsaknainta da Hameeda cewa take ko kowa ya nuna Mata naqi a bangaren Mama ita kadai zata tsaya a bayanta duk runtsi duk wuya saboda a baya ba Mai cin fuskar ta a dakin Mama makukar tana gurin Koda kuwa mamar ce, Amma yau Hameeda da bakinta Kuma a gaban idonta take fadar magana irin wannan, to meya canzata daga Hameedar data sani Mai sonta da kaunar ta da Bata kariya da kulawa a kowane janibi. Saida tayi Mai isarta har ta baiwa uku lada, sannan ta hakurkurta da Kanta ta tashi zaune. Kanta taji ya Sara Mata a hankali ta furta "Alhamdulillahi ala kulli halin. Allah na gode Maka duk abinda kayi nufi a gareni na karba ka bani ikon cinye jarabawar Nan dan isar Annabi Muhammad s.a.w.w". Hannu tasa ta dafe Kanta dake matukar Sara Mata, wannan wace irin rana ce a gareta? ranar da duk wasu masoya keda tarin burika a Kanta Amma ita ranar ta ta farko ta kasance ranar cin fuska daga inda Bata taba zato ba, ba tarairaya duk burin da suka dade sunaci na irin wanna ranar ya tashi a banza. "Astagafirullah Ubangiji ka yafe min zunubina daya janyo min irin wannan rayuwar Mai tarin qalubale a cikinta". Ajiyar zuciya ta sauke tana Kara dafe Kanta da gaske jinsa take Kamar ze rabe gida biyu, ba zato ba tsammani taji an bude kofa Bata daga Kai taga ko waye ba dan kamshinsa kadai ya Isa ya fada Mata Mai shigowar, Kuma ma waye ze shigo haka Kai tsaye a irin wannan lokacin, sallama yayi Mata Amma Allah baisa ta amsa Masa a fill ba ta dai amsa a zuciyar ta. Takowa yayi a hankali har zuwa inda take zaune, har lokacin Kuma Bata daga Kai ta dube shi ba farar ledar dake hannunsa ya aje kusa da ita ba tare daya tanka Mata ba ya juya ya nufi kofa yana juya baya ta dago da sauri ta kalli bayansa kananan Kaya ne a jikinsa sabanin dazu da yake sanye da wani lallausan yadi fari tas da hula, sai taga Kamar yafi kyau yanzu akan dazun, kananun kayan sunfi karbarsa akan manyan da yake sakawa, hannun daya saka ya Kama handle din kofar idonta ya Kai taga hannun wani fresh dashi Kamar Mai rayuwa a kasashen sanyi. Ganin Kamar ze juyo ne yasa tayi saurin kauda Kanta Dan kada ya kamata da wadannan idanun nasa tana kallonsa. Kofar tabi da kallo bayan ya fice a hankali ta sauke ajiyar zuciya da gaske fa mutumin Nan yana Mata wani irin kwarjini, ga wani tsare gida naba gaira ba dalili da yake saiya karta Abu ya wani maze Yana Shan kamshi. Karan bude kofar ne ya dawo da ita daga tunanin data shiga na wucin gadi, kusa da ita ya zauna daf da daf dan ji tayi Kamar numfashi daya suke sharing dashi, a hanakli yasa hannu ya dago fuskarta data Kama idon ta rufe, a zuciyar ta tace "na bani ni Fatima shi Kuma kome faskar Nan tawa tayi Masa? shi dai ya taba jikina kawai ya sani, muryar shi ta jiyo cikin deep voice yana fadin "Pls open your eyes and look at me mana". Kai ta shiga girgiza Masa alamar a'a. Shi abin nata ma mamaki yake bashi, a ranar da suka samu wannan arangamar da ita soron gidan Baba malam yaga ta rufe idanu ya dauka ko tsabar razanar zata fadi ne. Amman sai yaga abin na neman ya Zamar Mata jiki indai zata ganshi to kuwa sai ta rutse idanu Kamar taga wani abun tsoro, a haka zasu rayu da ita ai baze yuwu ba gaskiya dole yayi wani abun daze cire koma meye yake haddasa Mata hakan a tare dashi. "Ok Ashe zamu kwana a haka kenan tunda bazaki bude idanun ba, ko Kuma wallahi na shayar dake mamaki yazun nan". Shiru tayi Masa kirjinta Yana fat, fat da sauri kusancin yayi yawa duk ya kanainaye ta. Batayi zato ko tsammani ba taji harshensa akan fata idonta Yana lasa yana busa mata iskar bakinsa kamshin Lister mint mouthwash Yana dukan fuskarta ciki Shirin fita hayyaci tayi baya da sauri ta fada kan gadon da baya idanun nata tar akan fuskarsa da yana mata wani Yana Mata wani kallon kasa - kasa nan da Nan taji tsikar jikinta tana tashi sai hawaye zurrr... "Why! meyasa? Ai da sai ki barni na kwashe abinda yake hanawa kina kallon nawa Mana, oya tashi abinci zakici bazaki kwanta da yunwa ba kisa na Fara karya Alkawarin dana daukar Iyayena na kula dake,dan kowa amanarki yake bani da jaddadda min na rikeki da amana da gaskiya cikinsu harda bestien mu kuwa". Ya fada a kasalance Yana kashe Mata ido. Sai Kuma ya dan zamo kadan ya dauko plate Wanda ita Sam Bata San lokacin daya ajesu a gefenta ba, ledar ya bude wani kamshi ne ya doki hancinta Mai shegen Dadi kaza ce wani irin gashi akayi Mata Kamar na tsire da vegetables a ciki ya juye Yana fadin. "Oya tashi kici kafin ki kwanta kinsan yunwar dare tana kawo ciwon ulcer,kada ta kamaki ace Ina barinki da yunwa ni d'an malam gara na Kara kiwataki duk wanda ya ganki ace Masha Allah! Kamar ba matar Almajirin Baba malam ba". Ya fada da alamar zolaya a karshen maganar tasa. Itafa Yana Bata mamaki wallahi zata iya rantsewa idan aka saka Masa hannu a Baki baze ciza ba amma dubi yanda ya wani zage yana magana Kamar bashi ba. Ganin da gaske zata Bata Masa lokacin shi Kuma Yana da abinyi da yawa yasa ya matsa sosai kusa da ita ganin Yana nema Kara mannata a jikinsa yasa tayi saurin tashi zauna tana kikkibta idanu tana kallonsa. Da hannu ya nuna Mata plate din, cikin Rashi kuzari a maganar tata tace Masa "na koshi bazan iyaci ba kaina ciwo yake". Ta fada murya a shagwabe ga daman tasha kukanta. Sai yaji ta Kara bashi tausayi abun ne yayi Mata goma da ashirin. Cikin sigar lallashi yace. "To kici ko kadan ne saina kawo Miki magani kisha kinji" Ya fada yana Kara nuna Mata plate din da idonsa, kadan taci duk a takure shi har mamaki take bashi a yanda yake ganinta ai ta wuce ace tana jin irin wannan kunyar ko tsoron irin haka, tunda da gani wayayya ce ta ajin karshe, ga Kuma yanda ta ringa ta'ammali da samari kala kala, a yanda yaji labari fa sau uku ana fasa aurenta Wanda ba Wanda yasan dalilin hakan, yasan kawai rainin hankaline irin na Mata, yanda zamanin ya Zama abinda ya Zama Amma dai ai gaskiya zatayi halinta komai daren dadewa. Ba laifi ta danci tace masa ta koshi tana kokarin fitar da kwalla. A zuciya yayi yana jinjina saurin kukanta Kamar wata 'yar goye Sam yaga kuka ba wani wahala yake Mata ba, tana kuka tun abun kukan Bai Samu ba to idan ya samu yaya za'ayi kenan?. Kwashe kayan yayi ya fita dasu Bai jima ba ya dawo da p.c.m tablet a hannunsa da ruwa marar sanyi, farm fresh yogurt ya Fara zuba Mata ta karba Tasha sosai dan tana sonta sosai lokacin tana Jos har kamfanin take zuwa ta sawo musu, tayi Mata Dadi sosai sanyin moderate ba Mai cutarwa ba. Saida ya tabbatar da tadan samu relief kafin yace Mata. "Ki tashi ki canza kayan jikinki ki kwanta idan kikayi barci kan ze daina ciwon, in Sha Allah, Kuma na fada Miki tun kina Asibiti ki rage damuwa Bata maganin komai sai Karin matsala Amma idan Kika hakura komai Mai wucewa ne Zaki sameni fiye da yadda Kika tsammmata kiyi hakuri komai da Kika gani hukuncin Allah ne ba Wanda ya Isa ya canza idan Ina tunani akan kaina na duba yanda connection din ya faru nasa ba Wanda ya Isa ya tsara haka sai Allah Dan haka ki Barbi abinda ya Baki Koda bakya so kinda ance wani hanin ga Allah baiwa ne tunda gashi ya Baki Dan malami sukutum ai tsakaninki da Allah sai godiya". Ya fada Yana kafeta da idanunsa masu sakata ladabin dole. Kai kawai ta gyada Masa, ba baka sai kunne, mikewa yayi da cup da robar farm fresh din a hannunsa ya nufi kofa a hankali ya juya very lockly suka hada ido kashe Mata ido daya yayi Yana Dan murmushi Wanda Batasan Kona menene ba, sannan yace Mata "good night". Yaja kofar wasu sabbin hawayene taji Kuma ita harga Allah bada niyya ba jinsu kawai tayi hakika tana tausayin kanta, da gaskiyar masu iya magana da suke cewa cusa Kai ba kwarjini yawa ne yau ta gani ganin idonta Wai ita Amarya ce wadda zayati kwanan farko a gidan miji. "Ya illahiy!!! Wannan wace irin ranace haka? Yanzu da Musba.... Astagafirullah". Ta fada da sauri tasan tunanin wani irin haka haramun ne da aure a kanta. Ta jima a gurin tana sakawa da kwancewa Amma dai duk inda ta juya amsar daya ce aikin Gama ya riga ya gama sai hakuri da zubawa ikon Allah ido Dan shine alimil gaibi. Tunda Mahmud ya shiga nasa bedroom din ya kasa samun nutsuwa Banda yayi namijin kokari ya kauda kansa da lallai sai ya rage zafi gaskiya idan yayi haka baimata adalci ba. Dan shi a nasa bangaren kamai ya gama zamar Masa daidai, saidai ita uwar gayyar batasan wainar da yake toyawa ba dan idan da abinda shi Kuma Bai lamunta ba yayi Mata dole yafison komai Daren dadewa taso shi da muradin kanta yafi son ya koyar da ita yanda zata soshi fiye da kowane da namiji data taba so a rayuwarta, ba Kuma ya son tasan koshi waye bama ita ba kowa ma dake tare dashi a nan, yafi son ya Gina kanshi a gurinta a wannan matsayin na yanzu. Wanka yayi ya saka pyjamas dinsa farare sol nasu laushi, yana jinsa cikin watan irin nutsuwa, maimakon ya kwanta sai ya dauko laptop dinsa ya dosa aiki sai gurin biyu da kwata ya ture computer din ya tashi ya nufi kofa ya fita dakinta ya nufa dakin zahrar yana zuwa yana turawa yaji kofar a bude Kuma dakin da haske yayi zaton ko barci ne ya dauketa tabar wutar Mai haske a kunne. Yana turawa ya ganta akan sallaya tayi sujuda Amma shashhshekar kuka take Allah kadai yasan abinda take roko tsakaninta da mahalicci ya jima a tsaye kafin yaja Mata kofar ya fita jikinsa a matukar sanyaye dan ba karamin qima ta kara a idonsa ba ya Kuma Kara godewa Allah da yayi Masa kyauta da wannan yarinyar yasan Allah sami'uddu'ai ne yasha raba dare Yana rokon Allah ya bashi mace ma'abociyar addini, sai gashi a inda Bai taba zato ba Dan gaskiya Bai taba kallonta a wata mujahida ba yafi Mata zaton bokon ya rinjayi bangaren islamar ta. Koda ya koma shima Bai kwanta ba Saida yayi nafilfili sannan ya kwanta da tunani kala-kala a zuciya. Hudu da minti arba'in ya farka ka'idarsa kenan ta tashi sallar Asuba, wanka yayi ya saka jallabiya milk colour ya bude kofa har ze wuce sai yaga Bai Dace ba gara ta tasheta ta. Sanda ya tura kofar har ta Fara raka'atanul fajri ta Riga ta tashi, lallai ya jinnina Mata gurin ibada sai yaji ya qara samun wata nutsuwa a tare da ita da sauri yaja Mata kofar ya nufi falon jin za'a tada sallah.l ✨✨ ✨✨ 🔷AUREN HUCE HAUSHI 🔷 ✨✨ ✨✨ MAMAN FATIMAH 💎 PAGE NINETEEN 💎 (19) AssalamuAlaikum warahamatullahita'ala wabarakatuhu. Ina mika sakon jaje gan Alummar maiduguri bisa ibtila'in daya samesu na karyewar Alo dam, Allah ya jikan wadanda suka rigamu gidan gaskiya Wanda Kuma suke gida da Asibiti Allah ya basu lafiya, abinda aka rasa na dukiya Allah mayar musu da ninkin abinda suka rasa. _______________Mahmud tunda aka idar da sallah Bai shigo gidan ba sai kusan karfe shida da rabi, ya Dan jima da Mai gadi kafin ya shiga ciki dakin Zahra ya nufa a kwance ya sameta akan sallaya da gani batasan lokacin da barci ya dauketaba yasan kusan kwanan zaune tayi, a hankali ya matsa daf da ita Yana karewa fuskarta kallo idanunta sun dan tasa alamun kukan da tasha da Kuma rashin barci, wayarta ce a gabanta a kunne tsugunawa yayi ya dauka Qur'an ya gani tana karantawa barcin yayi gaba da ita, baiyi tunanin tashin taba kada ya katse Mata barcinta. Kan stool na madubi ya zauna da wayar a hannunsa Yana dubawa haka nan yaji Yana son ya shiga ya duba received calls da missed calls nata, a hankali ya ringa bi Yana dubawa yawanci kawayenta ne sai Kuma Ummee da ya gani har ze aje sai yaga Kamar number din guyn da zata aura Dan lokacin daya tafi da wayarta ya canza mata wayar da sim card din a Nan ya haddace number din tasa sai Kuma yanzu daya ga Kiran jiya dai dai lokacin suka bar gurin Baba malam, Nan da Nan yaji ransa ya sosu duk da Kiran daga gurinsa ne ba daga gareta ba. Tashi yayi tsam yabar dakin da wayar a hannunsa shima kwanciyar yayi, can cikin barci yaji alamun ana Danna door bell da kyar ya tashi ya nufi kofa, Musaddiq ne da Faruq din Aunty Hasana suke kawo break fast cikin ladabi suka gaishe dashi ya amsa yana Basu hanya suka shigo da basket din dake hannun Musaddiq ya Dora akan dining table. Musaddiq ne ya juya ya nufi kofa yayin da Faruq yayi tsaye, har Musaddiq yakai kofar fita daga falon ya juyo Yana fadin "Faruq me kake jira ne ka tsaya? kasan driver Yana jiranmu fa".. "Taya zamu tafi bamu gaishe da Aunty Zahra ba?". Mahmud ne yace "Faruq Auntyn barci take sai dai zuwa anjima sai ku dawo kaji". *** Cikin damuwa da matsanancin tashin hankali Mama ta tashi, tunda garin Allah ya waye ta tasa kayan da Hameeda ta shigo dasu jiya a leda da envelope din kudin da mijin Zahra ya Basu a gaba ko bakasan kayan kwalliyar Mata ba kaga wadan Nan kasan ba Karabiti bane ga uwa uba kudin daya lafta musu ita abin har ya Fara Bata tsoro, dan a zahiri kowa yasan fakiri ne wanda Bai ajeba bai bada ajiya ba amma a badini abubuwan da yakeyi suna da ban mamaki. Wayar ta ta dauko tayi dealing din wata number ba'a Dade ba aka daga Bata koyi sallama ba ta Fara magana "Asabe kome kike kizo anjima da matsala babba komai Yana neman ya dagule fa kizo kiga abinda wancan tsintacciyar magen ya baiwa su Hameeda jiya harda fadin magana dan Hameeda ta fadin maganganun danace ta fada wallahi Ina kokonto akan lamarin yaron nan Dan jiya da dare Dana Kira malam na BANDE cewa yayi Wai mun kuskure wani abu shi yasa har Alhajin ya iya daura mata auren Kuma yayi duk iya yinsa ya kasa ganin komai akan mijin nata sai wani haske kawai yake gani". Daga can taji magansr mamar ta amsa da "hakane ba damuwa sai kinzo din ta aje wayar tana jan karamin tsaki ta tashi ta shiga toilet. A bangaren Ammah kuwa bayan Sajida da zulai sun Gama aikin break fast din da aka Kai gidan zahra, sajidar wanka tayi ta Shirya kafin ta fito falo su karya, bayan sun Gama ne ta kalli Ammah tana fadin "Ammah in Sha Allah yau an tafi gida Ina son na wuce school ne daman na jira ne saina raka Zahra gidanta tun last week muka Fara lactures". Ta fada a ladabce. "To Babu laifi hakan Allah yayi Albarka, sai Magaji ko Malam Bala wani ya Kai ki mun gode madallah, kunyi sallama da mutuniyar tun jiya kenan!" Ta tambaye ta. Kai ta girgaiza tana fadar "A'a sai anjima zan shiga muyi sallamar". ___ Zahra Bata tashi ba sai wurin takwas da rabi tayi Mika gami da salati tana Kara ware idanu tana kallon dakin da alama kamar ma ta manta inda take Sai a hankali ta dawo cikin nutsuwarta "ya Salam". Ta furta hankali tana ware sexy eyes dinta, wallahi Sam ta Manta da waifa a dakin gidan aurenta take ba a dakin Ammah ba, tashi tayi zaune kan sallayar tana Kara kallon Kanta har lokacin hijabin da tayi sallar ne a jikinta. Toilet ta shiga duk jikinta ya Mata wani irin nauyi Sam Bata jin dadin jikin nata ruwa Mai dumi ta hada ta shige ciki tayi kwance tana shakar kamshin turen wanka data zuba ta jima sosai a cikin ruwan kafin tayi wanka ta fito sabon towel ta dauko mai kalar purple Babba ta daura ta fito gurin mirror taje lotion ta dauko ta shafa a jikinta, tashi tayi ta nufi gurin wata jaka kayan gyarab gashinta ta dauko, zuwa tayi ta zubesu yanzu da a gida ne da Ammah ce zata gyara Mata tsab ta hade shi guri daya, tana kiciniyar daureshi taji alamun bude kofa da sauri ta kalli gurin, Mahmud ne cikin shigar kananan Kaya yayi wani irin fitinannan kyau, hannunsa ya nade a kirji ya jingina da kofar ya zuba Mata idon dake figitata, shi be shigo ba shi be koma ba ya kafeta da idanunsa. Tunda suka hada ido dashi tayi saurin sunkuyar da Kanta jikinta na wata irin rawa duk ji tayi ta rasa yanda zatayi daga ita sai towel din Nan a jikinta, gashin ta saki ya bazu har gadon bayanta ta matse hannunta a kijinta, sun Kai kamar minti uku a haka Yana Kare Mata kallo son ransa a cikin zuciyar sa Yana tsarkake sunayen Allah da yayi Masa kyautar bazata da wannan kyakykyawar halittar dake gabansa a matsayin matarsa ta sunna halaliyarsa wadda ba wani shamaki a tsakanin su. Cikin takunsa Mai Cike da karsashi Amma a nutse, ya doso inda take tsaye Yana zuwa ba zato ba tsammani taji ya saka hannu Yana tattaro gashin daya bazu a kafadarta yana fadar "Bari na gyara Miki tunda Naga yana neman gagararki". Bata iya ce Masa komai sai jikinta daya cigaba da tsuma, tsab ya hade ya saka ribom din daya gani a kusa mayukan gashin brush comb ya saka ya Kara gyara shi sannan yayi baya a hankali ya zauna akan sofa Yana fadar "ki shirya kizo muje ki bamu break fast gashi can Ammah ta aiko tun wurin 7:30 su Musaddiq suka kawo". Bata amsa ba Kuma ta dago kalle shi ba, d'an gunguni ta fara kasa kasa "kawai ka zauna mun a daki kana kalleni kaki fita a gabanka kake son na saka kayan ko me?". Yana kallonta gefen ido tana magana a ciki baya raba daya biyu yasan complain take akan zamansa. Tashi yayi Yana fadin "idan kin Gama kiyi min magana Ina aiki ne". Ya juya ya fice. Wata ajiyar zuciya ta sauke tana fadar "innalillahi ni Fatima Naga ta kaina Wai shi wannan waye shi? Nifa wallahi lamarinsa sun fara bani tsoro gaskiya" ta fada tana cuno Baki, sai Kuma tayi sauri har towel din jikinta na neman faduwa key ta sawa kofar, a gurguje ta saka doguwar rigar lace peach colour Mai touching din flowers green Bata daura Dan kwalin kayan ba saita rufa gyale green,Sam batayi wani make up ba powder kawai ta shafa sai lips glow turarenta ta fesa ta nufi kofa ta bude ta fice tsaye tayi a cikin corridor din saita rasa a wane bedroom din yake. Ta jima a tsaye tana saka yanda zata tunkari dakinsa Kai tsaye, cikin yin shahada ta nufi inda take zaton nan ne bedroom din nasa a hankali ta murda handle din ta tura kamar wadda za'a cewa ket ta ruga, wani sanyi da kamshin turensa Dana freshner ya shiga hancinta dakin ba wadataccen haske duk curtains din windows a sake suke can kan sofa ta hango shi da laptop a gefen sa yana ta faman daddanabawa tsaye tayi ita Bata shiga ba ita Bata koma ba, yana kallonta ta gefen ido Amma sai ya basar kamar bai ganta ba. "Assalamu Alaikum". Ta fada a darare, Bai kalleta ba Amma ya amsa sallamar. Dan Jim tayi kafin tayi karfin halin cewa "na gama shiryawar". Kansa ya dago ya kafeta da idanunsa da yake razanata dasu kafin yace "idan bazaki shigo kije kawai an fada min Ina cinye mutane ne da Kika tsaye a nan". Dan cuno Baki tayi ta saki handle din ta shigo a nutse Amma fa Babu nutsuwa Kota sisin kwabo a zuciyarta ta ayyana "waya sani ko mayen ne tunda abune a duhu". A tsakiyar dakin ta zauna an carpet Kanta na kallon tace Masa "barka da Asuba". Shiru yayi kamar Bai jiba Saida ya Mula dan kansa yace "Lafiya ya kwanan bakunta I hope ba wani damuwa ko?". Kai ta gyada masa alamar eh. Yace "good Bari na karasa wani dan aiki muje muyi break ko?" Ya fada Yana kallonta. Ganin tayi shiru yasa yaci gaba da aikinsa ita Kuma tana zaune duk sanyin dakinsa ya Mata yawa, tana son sanyi amma sai taji na dakin yana neman ya sakata rawar jiki. Baifi minti biyar ba ya rufe laptop din ya Miki, gurin da take zaune ya nufo yana zuwa ya Dan tsuguna kusa da ita Yana fadin "taso muje kada nabar 'yar amanata da yunwa na amsa query a gurin su bestie ko?" Ya fada Yana murmushi. Hannunta ya kama ya dagota tsaye suna shakar numfashin juna Amma ita kanta yana duban kasa, dayan Hannun yasa ya dago fuskarta as usual yanda ya saba. Ajiyar zuciya ta sauke a hankali Amma bata rufe idon ba kamar yanda ya hanata a jiya Bata manta ba amma ta kauda Kai gefe dan da gaske Bata iya had a ido dashi. Dan kwanto da ita yayi jikinsa Yana juyo da fuskarta yana fadin. "Wallahi kada ki rusa min budget dina kisa na kwashe kunyar nan daga idanunki tun banyi niyya ba matukar zakici gaba da irin wannan dabi'ar". Das das girjinta ya kara bugawa akan wadda yake, tana fadin "oh ni Zahra tawa ta sameni shi Wai wane iri ne haka? sai yayi ta sakin magana ko kunya babu". Saida ya matsa mata taci abincin kirki bayan sun Gama ne suka dawo parlor suka zauna Sam Babu sabo ko kalilan a tsakaninsu kallo ya kunna a Nile sat ya kamo super support suna kwallo live. Ganin ita ba wani gane kan ball din take ba yasa ta Mike zata koma daki ta kira Sajida taji ya maganar tafiyar Dan tun jiya da Abba yace a jiya zata tafi gidanta sajidar tace itama sai gida ta. Takunta biyu taji ya janyo ta ta fada jikinsa ba Shiri ta zaro ido waje hura kata iskar bakinsa yayi a fuskarta dalilin yasa ta rufe idonta kenan a hankali yace "Ina Zaki ki barni a zaune alhalin saboda na tayaki Zama yasa naki fita ko ina". ✨✨ ✨✨ AUREN HUCE HAUSHI ✨✨ ✨✨ 💎 PAGE TWENTY 💎(20) _______"ya Salam". Zahra ta fada a hankali jin yanda yake hura mata iskar bakinsa a fuskarta, yasa hannuwansa duka biyun ya tallabo fuskarta yana kallon face din very cute da ita, shifa baya gajiya da kallonta komai nata burgeshi yake yi Dan bakinta ya kalli 'yan kyawawan lips din ta pink, gdy yake yiwa buwayi Gagara misali daya mallaka masa ita a lokacin da bai taba zato ba, tunda ya kafeta da ido Bata yarda sun hada ido ba, ba Kuma tayi gigin dogowa ba. Qaran da door bell din tayi shiya kawo karshen 'yar tutsiyen da yayi Mata wani soft kiss ya yiwa gefen wuyanta Wanda har Sai da ta zabura tana fadin "wayyo Allah!". A shagwabe ta janye jikinta daga rikon da yayi mata, shi Kuma ya tashi ya nufi kofa, Bata jira taga waye ba tayi wuf ta nufi ciki jikinta kamar mazari. Tana shiga ta zube a gado tana fitar da numfashi da sauri da sauri kamar wadda tasha gudu, jin alamun bude kofar yasa tayi saurin duba gurin Sajida ta gani tsaye ta tsura Mata ido tana Mata wani kallo cikin mutukar tsantsar farin ciki zahrar ta taso tana fadin "haba bestie kin wani tsareni da ido kina min kallon qurillah irin wannan ko Kinga wani abu a jikina ne?". Ta qarasa fada tana karasowa kusa da ita 'yar madaidaiciyar ledar hannunta tana fadar "Wai meye Kika wani yi shiru kina kallona ne Dan Allah talk to me Mana pls". Biyo bayan zahrar tayi har gefen gadon kafin ta samu kuzarin fadin "Bestie Kinganki kuwa just one day Amma har kin Fara canzawa, Fadi min meye sirrin gaskiya, na tafi jiya da zulumin ki a Raina yau kuma nazo na sameki haka kin wani Kara Zama fresh dake". "Bestie tsakanin mu harda 'yar zolaya zakice Wai na Kara zama fresh?" Zama tayi gefen zahrar tana fadin "wallahi I am serious kin canza a idona gaskiya Kinga ai dole na fada ko?". "To shikenan kin fada bazan hanaki ba, wai da gasken yau Zaki wuce?" Kai ta gyada Mana kafin tace "In Sha Allah meya rage kuma ai gara naje na fuskanci karatun ko tunda na samu nutsuwa kin shigo gidan ki. Alhamdulillahi, ga sauran abubuwanki na wajen Baffan rimi kici baga da amfani dasu dazuma munyi waya da safe yace na bawa Ammah abinda ya Aiko dai ya Kara jardada Mata na a fada Miki kada wani ya kawo Miki abu kici Kuma yace a tura a karbo Miki sako Nan da sati daya". Dan langabar da Kai tayi tana Kara ganin kimar Sajida ta dauki matsalar nan tata bada wasa ba. Godiya sosai Zahra ta yiwa Sajida akan abinda suke mata, sun Dade sajidar na yiwa Zahra nasiha akan ta rike aurenta da kyau ita bataga wani abun ashsha ba gurin Mahmud idan. Nan da Nan idon Zahra ya kawo ruwa ta shiga sharewa da hannunta tana fadar "wallahi bestie na rasa dalilin da yasa nake jin wani abu a tare dashi tun ranar Dana Fara ganin shi naji abun ko kallonsa fa nayi sai naji gabana Yana faduwa heart beat Dina Yana karuwa, kinsan ma inda matsalar take?" Kai sajidar ta girgaiza tana fadar "sai kin fada". "Kinsan haduwar mu ta farko rungumeni fa yayi a cikin jirjinsa tsam kamar.wata baby amman Kamar an dinke min Baki na kasa ko fada Masa magana ne saima wani azababben kwarjini da yayi min harda fadar na ringa kula kada nayi musu asara'. Ai Sajida Bata San lokacin da wata dariya ta kubce Mata ba tana fadar. "Babbar magana kice da wata tsumammiya a tsakani ku tun tuni har kika dauki alhakina gurin hanani kwanciyar hankali tun jiya Allah barci ma ban samu na kirki ba Ina zulumin abinda kaje yazo, Dan ba kowa bane za'a aje masa mace kamar ke ya iya kauda Kai gaskiya" Wani duba zahrar tayi Mata tana fadin "ban Gane ba me kike nufi da maganganunki?. Wata dariyar tayi tana fadin "A'a ba mefa nake nufi kawai dai...... " Sai tayi shiru. Wani zancen ta dauko Tana fadin "Zahra ki tsaya ki nutsu a gidan aurenki ki gyale kowa duk wanda ze raina Miki miji kada ki amince ko waye kuwa Koda ni da nake Miki wannan maganar, Kuma game da Hameeda ki kula sosai Dan a jiya ta nuna Miki jiya ba yau bace, jini kuma yafi ruwa kauri, Koda ta dawo tana neman Kara shiga jikin ki da wata manufar tazo, Dan Allah kiba marada kunya duk yanda ake son ganin lapses dinki kada ki bada damar hakan". In Sha Allah zan kula nagode Bestie Allah yabar zumunci. Zahra ta fada "Ameen" sajidar na ta fada, suna cikin hira akayi knocking din kofar ba'a bude ba Zahra ce Mike tana fadin "ina zuwa, tana kokarin yafa gyale ta rufe gashinta Sajida ta warce ta aje gefen ta tana fadin "haba ke kamar matar liman a daki na da Bata ja ba tayi gaba saboda an Kara buga kofar, budewa tayi Mahmud ta gani Yana tsaye ya canza kaya ya saka Riga da wando na wani yadi light brown dinkin buda yana baza kanshi sa na ibada. Matsawa tayi daga jikin kyauren ganin alamar shigowa zeyi Amma fa Saida yadan shafi fuskarta kadan sannan ya ida ahigewa ciki, tsaye tayi tana binsa da ido tana ayyana "Wai meye ne yake faman shafa mata fuska har a gaban mutane ko kunya bayaji tasan wlh sarai Sajida ta gani sai dai ta basar kawai gashi ta wani rike mata gyale ta wani barta tsurarta". Direct gurin mirror ya nufa ya zauna a Kan stool, Yana fadin "Bestien mu zuwa nayi muyi sallama naji Abdul Hakeem yana maganar Zaki wuce yau ko". Ya fada Yana murmushi, itama murmushin tayi masa tana fadar. ",In Sha Allah yau sai kano tunda Allah ya cika min burina Zahra ta shigo gidanta fine". "To mun gode kwarai Allah ya saka da Alkhairi sai munzo visiting idan madam zata dauki nauyin zuwan mu Kinga Nima sai Naga duniya ko madam?" Ya zubawa Zahra narkakkun idanunsa Yana Mata wani kallon qasa qasa. Shiru Zahra tayi tana yafa gyaren a kanta, Sajida ce tace "gaskiya Kam haka za'ayi". Tashi yayi ya Dan tako kadan zuwa gaban Zahra kamar ze hadeta da jikinsa da sauri tayi baya tana turo Baki yi yayi kamar Bai gani ba, envelope ya Mika mata Yana fadin ki Bata sskonta ne na jiya data Bari nayi niyya bazan canza ba sai dai idan bataso ta bayar, nizan shiga gurin su malam". A hankali tace "an gode madallah a dawo lfy". "Amin to bestie sai munzo ko". Bai jira abinda zata ce ba yayi ficewarsa. Ajiyar zuciya Zahra ta sauke tana Zama kusa da Sajida Mika Mata envelope din tayi tana fadin "yaushe ya Baki kikace bakya so?". "Jiya Mana lokacin da zamu tafi sanda wannan jikar marokan ta zubar da darajarta ta rokeshi, yanzu Dan Allah me Hameeda ke nema? wane irin rufin asiri ne Allah Bai mata ba. Amma ta lalace gurin roko? shi yasa na aje masa kudin sa nayi gaba kayan ma nace bana so su rike". Dan murmushi Zahra tayi tana fadin "Saji danger wato halin na Nan ko? To nidai gashi nan tunda a gaban ki ya bayar saiki karba". "Bude mu gani to" Sajidar ta fada. Stalling founds ne na ingila musu yawa a ciki kallon kallo sukayiwa juna kafin Sajida tace wallahi bestie akwai kukus a shinkafa zakice na fada Miki, Wai kuwa kin tsaya kin Kare guyn nan kallo kuwa?". Kinga ya Miki Kama da Wanda baida abinyi ko wanda ya tashi a cikin rashin wadataccen ilimi da mugu? Dubi muhallin daya ajeki, ance malam ya bashi gidan sai kungiyar da yakewa aiki sukayi renovation din gidan ki kiyasta nawa yaci gurin aikin kinsan da an kashe abinda yafi kudin ginin duk yi Masa akayi? Ki tuna Nan fa ba garinsu bane ance bako ne kuma yaki fadin garinsu anyi magana ance yace ya manta komai sai a hankali idan ya tuna hankali ze yarda da hakan? Kuma kina tunanin Abba ze daukeki ya bashi ba tare da yasan wani Abu a tare dashi ba? Kiyi nazarin abin Mana ni dai ina fada Miki kibi komai a hankali kuma yanda na fashimci wani Abu a maganar da Kika fada min kinfa kamu da son guyn Nan tun sanda kuka hadu ba tare da kin sani ba, Kuma Shima Naga yanda yake shige Miki ko kunya ta Bai jiba kinsan sai a hankali kawai kwanan Nan labarin ze sauya irinsu basayi da wasa fa". Ta garasa fada tana dariya kasa-kasa. Suna cikin tattaunawa Kira ya shigo wayar sajida "Ya Abdul Hakeem ne" ta fadawa Zahra kafin ta daga. "To" Kawai tace ta kashe Kiran tana fadin. "To bestie ya Abdul Hakeem Yana jirana Wai a she shine ze Kaini nifa daya fada na dauka da Wasa yake lokacin da Ammah tace Magaji ko Malam Bala dureba zasu kaini sai kawai yace su Bari Shima Yana son yaje kanon Sai ya tafi Dani". Dariya Zahra tayi tana fadin "idan tayi wari munji batun, yanzu ba fa Naga Ya Abdul Hakeem Yana dama dama dake ba bai fada min ba Amma zakice na fada Miki Ina ga target dinsa kenan yau yake son ya yad'a manufarsa shi yasa yayi Riga malam masallaci yace Wai daman kanon zaya". Kin magana sajidar tayi sai murmushi kawai. Zahra tace "bestie ko dai komai ma ya kankama ne ban sani ba Ina shirme?". Kafin sajidar ta Bata amsa wani Kiran ya shigo da sauri ta dauki jakarta tana fadin "To bestie sai gani na gaba Allah ya bada zaman lafiya ya kade fitina, sai anyi ta hakuri kafin komai ya dai daita ki kwantar da hankalin ki zakiji dadin Zama dashi in Sha Allah". Har gate ta rakata babbar ledar dake hannunta ta Mika mata tana Mata addu'ar sauka lfy. Amsa tayi tana Mata godiya ta bude gate din ta fita, ya Abdul Hakeem Zahra ta gani a mota a zaune cikin mamaki tace. "Ya Abdul Hakeem daman kana Nan waje Amma baka shigo ba?". Fitowa yayi ya karaso gurinsu Zahrar ta gaishe shi, sannan ta juya ta koma ciki duk zuciyarta ba Dadi Kamar ta Hana sajidar tafiya amma ba hali. ********* Mahmud Yana fitowa direct Famfon shanu ya nufa tunda lifan din Habib a gurinsa ya kwana, tun jiya daya karba da yamma Bai koma unguwar ba. Lokacin daya karasa yayi arba da motar Sameer wani murmushi yayi Yana fadin. "magulmaci kawai". Kafin ya shiga Saida suka dinga gaisawa da jama'a anata Allah sanya Alkhairi, Binya ya tambaya Ina Habib yace yaje Kai wani sako da malam ya tura shi ya Kai gidan sarki. Gurin Malam din ya shiga shi dasu Sameer ya samu suna magana da malam din Yana shigowa da sallama mlm din yace. "Yauwa Dan halak yanzu nake cewa bazaka jima ba zaka shigo, mutanen ku ne sukazo da wasu ayyuka gasu nan dai zasuyi maka bayani. Ya wajen iyalin naka!?" Dan sosa kansa yayi Yana Dan sadda shi qasa yace "Lafiya kalau tace a gaisheka" . "Masha Allah. Allah yayi Albarka" Gurin su Sameer ya juya suka gaisa, kafin suka fita zuwa inda suke meeting. Stepdown training zasuyi da school base management committee Basu tunda tsarinsu ya koma sun bin tsarin makarantun government ne sai kuma officially da suka gayyaci Mahmud zuwa gurin taron da zasuyi a Lagos nan da kwanaki biyar masu zuwa. Bayan Gama taron Sameer ya dauki Mahmud a mota suka fita hotel din suka nufa a hanya Sameer ya kalli Mahmud Yana fadin "yallabai meye labari naga text dinka komai an sawo zuwa anjima motar zata karaso amma sai nake ganin kamar kayi tafiyar nan da ita tunda zaka jima a can Kuma kaga duka kwanan ta nawa zaka tafin baka ganin abin ze iya Zama na surutu ko ace ma guduwa kayi amma dai ya kake gani?". Dan Jim yayi kafin yace. Tafiya da ita ba shine solution ba na dauketa na kaita Ina ko Kuma nace Mata wanene ni Nan nace Lagos zani can Kuma taga sabanin hakan ya kake tunani ka tuna fa she's educated, zatayi saurin gane komai ni kuma nafi son na Gina soyayya ta a zuciyarta ba tare da tasan who I am ba, I hope you understand?". Kai ya gyada Masa alamar eh. Sun Dade suna tsaya yanda program din ze kasance da abinda za'a batar da abinda za'a kashe a makarantar zuwa lokacin da zasu dawo suna cikin aikin direban daya dauko kayan ya Kira Sameer ya fada Masa ya shigo Azaren ya fada Masa inda yake tattara komai sukayi suka wuce gurin da direban yake, Sameer din ne ya shiga gaba direban na binsa a baya har zuwa gidan Mahmud din. Mai gadi ya taya direban sauke kayan, kayan abinci ne da sauran tarkacen girki hatta nama da kifi daga can aka kawo kayane masu matukar yawa. Ciki Mahmud din ya shiga tararwa ya yi tayi Baki har su zulai da sahura, a tsaitsaye suka gaisa yayi gaba zuwa bedroom dinsa. Ganin idon su zilan yasa zahra mikewa tabi bayansa dai dai lokacin Kuma Yara suka Fara shigon kayan masarufin da aka kawo, ganin zahrar Bata Nan yasa su sahura shiga dasu store din kayan abincin suka hada da wanda Abba yasa suka kawo dazu da kayan gara su gireba dasu dublan da alkaki. Sunyi mamakin yanda yara ke shigo da kayan abincin basu Kara Shan mamaki ba Saida aka Fara shigo dasu Nama da kifi ga drinks Nan ko ba'a fada ba Wai ance ido ba mudu ba amma yasan kima sun San kayan na manyan kudi ne, ko wacce da magana a bakinta Amma bata furta ba. Zahrar na shiga corridorn ta waske zuwa nata dakin. ✨✨ ✨✨ AUREN HUCE HAUSHI ✨✨ ✨✨ 💎 PAGE TWENTY ONE 💎 (21) ...............…... Sai da su zulai suka gyara Mata komai yanda ya kamata sannan suka gyara parlourn,lokacin da Mahmud ya fito bedroom dinta ya nufa baiyi wani knocking ba ya tura kofar a gaban gado ya ganta ta cire bedsheet din ta zubo da pillows din da alama wani Abu take nema sallama yayi mata cikin muryarsa Mai nutsuwa yana kallon ta, cikin takunsa na cikakken namiji ya karaso Yana tambayarta "lfy me kike nema ne haka Kika birkita gurin haka?". Jiki sanyaye tace Masa "wayata nake nema tun safe banganta". Dan matsowa yayi kamar ze tayata dubawar Yana fadin "Kuma tun safe Baki ganta ba Kuma Baki nema ba sai yanzu, to su waye suka shigo dakin ne?". "Shiru tayi kawai tunda tasan daga ita sai sajida ne a dakin Kuma tun bayan tafiyar ta ko Baki ne 'yan ganin daki Bata ahigo dasu Nan Dan gani take yaushe za'a dinga shigo da jama'a har dakin barcin mutum su dai dayan tunda ba a ciki take ba. Dagowa tayi ta Dan kalli gefen shi da gani wanka yayi ya canza kananun Kaya tana mamakin sa ita tunda take ganinsa Bata taba ganinsa da shiga irin wannan ba Kullum manyan kaya ne Amma daga jiya zuwa yau ya zamar Mata wani daban, Sam ba wancen bane take gani. Kamar ze wuce ta bayanta sai Jin Hannun Mutum tayi ya zagayo ta cikinta ya manna bayanta a kirjinsa ya kwanto da kansa dai dai saitin kunnenta iska yadan hura Mata kadan tare da hucin numfashinsa kafin yace. "Ki daina wahalar da kanki tana gurina tun safe na dauka, nayi mamakin da baki nemeta ba sai yanzu? Na cire sim din saboda Naga wani sakarai ya kiraki da number din to nasan ze iya bibiyarki tunda naga bashi da taushidi ko kankani Bai hakura ba da hukuncin Allah so yake da karfi saiya kwato abinda ya kubce masa". Kasa ko kwakwkwaran motsi tayi sanda yake jero Mata maganganun. Amma jin ya Kira Musbahu da sakarai marar taushidi yasa taji Zuciyarta ta wani baci, idan beji tausayinsa na abinda ya faru ba ai baze Masa bita da kullin irin wannan maganar ba, shida ya tsunci dami a kala har ya samu bakin magana irin haka. Nan da Nan taji ta samu wani courage wanda Bata San tana da shi ba, cikin muna bacin rai ta fara kokowar raba jikinta da nasa tana fadin. "Wallahi Musbahu ba sakarai bane, ba Kuma marar tauhidi bane,dan ya biyo abinda yake halalinsa amma kasan dai Banda qaddara ba abinda ze rabani dashi, dashi muka tsara planning na rayuwarmu Amma lokaci daya ka rusa Mana budget din mu ka yarda da aurena da aka baka Kuma wallahi tunda nake dashi bai ko taba rike ko hannuna ba, amma Kai kuwa fa ranar Dana fara ganinka a duniya dame ka Fara min bada rugumata ba?" Kai kenan baka da aikin yi sai tabawa mutane jiki ...... Bata karasa fadar abinda tayi niyya ba taji ya hade bakinsa da nata cikin zafin nama Yana ladabtar da bakin nata da harshensa, dayan hannun Kuma yayi Mata wani irin riko bana Wasa ba dayan Kuma yana yawo dashi a ilahirin jikinta cikin wani irin sarrafawa Mai zafi. Wata irin tsuma jikinta ya kama ga hawaye kamar na lalataccen famfo sai zuba suke ba bakin kuka sai mutsu mutsu take Amma ko a jikinsa wajen sau uku ana Kiran wayarsa tana tsinkewa, yayi biris da Kiran Kumar baya ji, sai da ya tabbatar da ya ladabtar da ita yanda yake so ya saketa, kan bed ta fada tana shashhshekar kuka hannunta daya yana Kan lebenta dake Mata zafi haka ma kirjinta zafi yake Mata ga gaban rigar ya farke Mata ita. Kafarsa daya ya doro Kan gadon dayar tana kasa ya Fara fadar maganarsa hankali kwance kamar bashi bane ya Gama yamutsa Mata jam'iyya yanzu ba cikin mugunta. "Wallahi na Kara Jin wannan sunan a bakinki ko magana makamanciyar irinta saina shayar dake ruwan mamakina, an fada Miki ni lusari ne da har Zaki tasani gaba kina fada min rubbish ne? an rusa muku budget din sai kuyi duk abinda zakuyi, an fada Miki Nima son abin nakeyi ne? da har Zaki tsaya kina min rashin kunya akan wannan lusarin Mai karairaya kamar mace,ke yanzu wannan har wani namijin arziki ne da ze iya dake? wallahi da kinyi tsautsayin aurensa da kin Gane Baki da wayo, idan Kika Kara gigin fada min magana makamanciyar irinta zan Baki mamaki wallahi, , har kike wani zakewa kina fadawa mutane magana, kice tak akansa billahil Azeem sai kin Raina kanki a dakin Nan saina banbance Miki tsakanin namiji da muna maza". Yayi tsaki ya juya abinsa cikin takunsa na ingarman namiji ya fice daga dakin zuciyarsa kamar zatayi bombing. A yanda su zulai sukaga ya fito Saida abin ya Basu tsoro kallon kallo suka shiga yiwa juna, sahura ce tace. "Zulai bakiga yanda Mai gidan nan ya fito bane? Allah yasa ba mutuniyar taki bace ta taboshi Kinga ai ba haka ya shiga ba". Zama zilan tayi tana fadin "waya sani sahura muna Nan tare dake, nifa shi yasa nace ba zanzo ba yau amman Ammah ta matsa akan sai nazo na Gane mata lafiyar ta,tun safe wayarta idan an Kira Bata shiga". "To Kinga kuwa dole ki dubota ki gani ko Lafiya ya fito a haka kofa a dawo lfyr mu bai amsa Mana ba". Jiki ba kwari zulai ta nufi bedroom din Zahra ganin zilan ta shige cikin corridor sahura ta Ciro wayarta Nokia ta Kira Mama. Ba bata lokaci ta dauka kamar jira takeyi ta shiga labarta mata abinda ta gani tun daga kan kayan da suka Zuba store har fitowar Mai gidan yayi da alamun bacin Rai a tare dashi, to kawai sahurar ke fada alamun wani Abu mamar take fad'a Mata sannan sukayi sallama. Sai da ya fice harabar gidan ya Ciro wayar daga aljihun wandonsa ganin Sameer ne yasa ya Maida wayar ya nufi inda Sameer din yake zaune cikin mota, Bai Masa magana ba, zagaya yayi ya shiga motar yana fadin "let's go" Ganin yanayin daya fito ya hana Sameer din korafin barinsa a waje baice ya shigo ba, dan kwantar da kujera Mahmud din yayi ya kwanta yasa hannu ya dafe kansa da gaske Sara Masa yakeyi lokaci lokaci Yana Dan Jan tsaki, Sameer dai be tanka Masa ba yasan a kusa yake, sai da sukayi nisa da gidan Sameer din ya Dan juyo yana tambayar. "Ina muka nufa yanzu nifa na gaji ga yunwa Ina ji kace muzo gida muci abinci Kuma ka watsar dani a mota inaga ma sai da ka rage zafi ni in Nan Ina hamma ka shanyani". Ya fada Yana Maida hankalinsa a titi. Tsakin ya Kara yi Yana dagowa daga kishingidar da yayi Yana duban Sameer din "Allah ya shiryeka ka dauka kowa ma irinka ne Wanda baya iya kauda Kai a Kan Mata? Muje can hotel din kayi order abinci kaci tunda bani na gayyato ka ba cewa nayi ka dorowa mota kayan Kai Kuma sai gurin jibi kazo, to bansan wane kinibibin ya kawo ka ba ka bar yarinyar mutane da ciki kana gantali". Ya karasa maganar Yana hararar Sameer din. Dariya yayi Yana "fad'in easy man bani na kar zomon ba rataya aka bani, waya fada maka lamarin su da sauki? bakaji abinda Abbanta ya fada maka ba? ai da yace sai ana hakurin da gaske ne Zama dasu Saida hakuri". Wani sakaran kallo Mahmud din ya aikawa Sameer da shi. "Ka wani zaqe kana ta zuba wani Abu nace maka tayi min ne? da kaketa faman fadin maganganu haka tsabar saka ido kawai, gobe ka tattara ka koma inda ka fito tunda ba gayyato ka nayi ba da zaka dameni da kananun maganganu zan shigo da kaina kanon ba ai ba bakuwa ta bace ba". Ya fad'a da gaske Yana Bata rai. Shiru Sameer din yayi ganin da gasken koma Nene yayi touching dinsa sosai. Suna shiga harabar hotel din kafin Sameer ya Gama parking a parking lot Mahmud ya bude ya fice abinsa Yana picking din wayarsa da aka Kira. ******Tunda zulai ta doshi kofar bedroom din Zahra take jiyo Kamar shashhshekar kuka, hannunta har rawa yake gurin bude kofar Dan ba maganar knocking, rubda ciki ta sameta tana faman shashhshekar da sauri ta mayar da kofar ta rufe ta karasa gurin zahrar da sauri tana Fadin. "Subhanallahi uwar dakina me zan gani haka me kikayi masa? Dukanki yayi? Dan Allah kiyi magana Kona Kira Aunty Hasana ne sai ki fad'a mata ko na Kira Miki Ammah". Kai ta girgaiza mata alamun a'a, "to ki fad'a min ko zan iya yi Miki wani abun Mana". Saida kukan ya lafa Mata sannan ta yunkura ta tashi zaune ido zulai ta zuba Mata ita ba yarinya bace kallo daya tayi Mata tasan da wata a kasa ganin yanda take a yamutsa ga labbanta sunyi jajir abinka ga farin Mutum ga gashin kanta duk gyaran ya turje. Zama tayi kusa da ita sai a lokacin taga gaban rigarta a yage Hannun bra dinta guda a tsinke. Kai kawai zulai ta dafa tana Fadin "mezan gani haka ni zulaihatu! Haba Zahra'u me yayi zafi haka ai sai kisa ya illataki a banza, gardama kika yi Masa yayi Miki haka?" Cikin shashhshekar kuka tace "A'a maganar Musbahu yake min shine ya Fadi Abu marar Dadi a kansa shine kawai Dan na mayar Masa da amsa Nima yayi min haka". Ta karasa fad'a tana kuka. Kasake zilai tayi tana duban zahrar kafin tace "Haba Zahra'u da wayonki da hankalin ki Zaki rinka irin wannan abun har yaushe Zaki ringa maganar wani namiji a gaban mijinki har kiyi ikirarin fad'a Masa magana marar Dadi akan shi ai yayi Miki kadan wallahi idan wani ne yau basai gobe ba saiyayi Miki kaca-kaca yanda ko sunansa ba Zaki Kara fad'a a gabansa ba, kada ki kuskura ki Kara irin haka Zaki ragewa kanki kima da daraja a idonsa, duka yaushe akayi daren da shashshawa zata Bata,Ina cewa jiya aka kawo ki amma ace an Fara da haka kinga abin baiyi kyau ba ko kadan, yanzu ki tashi ki shiga kiyi wanka da ruwan dumi zanje na cewa sahura kina wanka ne, mu tafi kawai tunda nasan halinta Abu kadan zata fara yaya tashi tunda nasan badan Allah ta biyoni ba dan Saida na fito harabar gidan ta biyoni. Sallam zulan tayi Mata Tana Kara tausarta akan ta ringa tauna irin maganar da zata ringa fada masa. Cikin karfin Hali ta Mike ta nufi toilet da gaske ya tsumama mata jiki ta jima a toilet din tana kuka maganganunsa sun Mata ciwo matuka har wani gori yake Mata Shima ba sonta yake ba, to an fada masa ita son nasa take har yake wani Mata wulakanci, ita ta rasa a Ina ta kuskuro ne take haduwa da fitintinu daga wannan sai wancan? "Astagafirullah". Ta fada a zuciyarta, alwala ta dauro ta fito ba wani kwalliyar azo a gani tayi ba duk ranta a cunkushe ga 'yar wayar da zata debe mata kewa ma ya dauke, a ranta tace "mugu kawai wani sumumu kasam dashi Kamar na Allah Nan kuwa dan duniya ne Mai lasisi". Tana cikin saka kaya taji karan bell alamun Baki a gurguje ta ida yafe gyalen rigar ta dan fesa turare tayi gaba. ***** Sai Bayan sallar magriba su zilai suka karasa gida dai dai lokacin Magaji ya fito da manya warmers a hannunsa sai Autan Ammah da basket a hannunsa Shima, zasu kaiwa zahra abincin dare. Suna shiga zilai ta wuce part din Ammah ta fada Mata sun dawo ita Kuma sahura ta nufi nasu bangaren sai da zulan ta shige part din sannan sahura tayi wuf ta shige sashen Mama. Salma kawai ta samu a falon tana kallon series na India ko arzikin amsa sallamar sahurar Bata samu ba sai wani kallon banza tayi mata tana Fadin "lafiya Kika wani shigo afujajun haka?". Kafin sahura ta samu zarafin Bata amsa Mama ta fito daga bedroom din ta tana Fadin Kamar maganar sahura nakeji?" Cikin azarbabi tace "nice Mama mun dawo". Ta fada tana Zama a kasa kan carpet. Cikin kwarewa da munafurci ta shiga korawa mamar bayanin abinda ta gani harta Kara da cewa. "Anya Mama yaron Nan kuwa Babu abinda yake boyewa kin ganshi kuwa? Gaskiya wallahi baiyi kama da fakiri Mai neman abincin yau da gobe ba, kayan abincin da muka zuba a store din wallahi ni wani abin ma ban taba gani ba hatta madara wannan manyan gwangwwnaye sunfi ashirin Nama kuwa na kaji kawai sun Kai hamsin Banda na rago Banda na shanu Banda kifi Allah Mama Saida muka cika freezer din cikin kitchen din ga lemuka da ruwa Kamar banza ga...... Bata Bari ta garasa ba ta daga mata hannu "bar shi kawai jeki zan nemeki". Mikewa tayi tana Fadin "a huta lafiya Bari naje nayi sallah naji ana Kiran insha'i". Ta fice. Tunda ta fita Mama ke jijjiga Kai tana kwafa, Sam hankalin salma na can gurin kallon ta Bata damu da abinda su mamar suke ba, Saida mamar ta Kira sunanta sannan hankalinta ya dawo Kan mamar tasowa bayi ta dawo kusa da ita tana fadin. "Mana menene Naga kamar ranki a bace,?". Tsaki tayi tana fadin. "Anya Abbanku da Asma'u ba ninkeni sukayi a baibai ba kan auren yarinyar Nan? ni daman tunda naga daga b'angaren Asma'u da 'ya'yan ta da 'yan uwa ba wata turjiya nasan da abinda suka taka bakiji labarin da sahura tazo min Rashi ba?". Kai salmar ta girgaiza alamar bataji ba, Nan Mamar ta shiga fad'a mata abinda sahurar ta fada Mata, Nan da Nan hankalin salma ya tashi ta shiga fadar "ai laifinki ne Mama Nan nazo na fada Miki naga wani inaso a gurin Baba Malam Kika dinga zagina duk yanda naso ki fashimceni shi ba irin wanda kike tunani bane ni naga abinda na gani Amma Kika shafawa idanunki toka kikaki saurarena ai gashi nan duk fafutukar ki ta tashi a banza ko yanda kika fada min gidan yake ai kinsan da wata a kasa". Ta fad'a tana share hawaye, Nan da nan hankalin Mamar ya Kara tashi idanunta sukayi jajur, cikin kaushin murya ta Fara fadar. "Ni za'a yiwa haka wallahi sai dai kowa ya rasa Dan wannan auren sunansa matacce dole ya saketa ko baya kaunar Allah ai indai Ina raye yarinyar Nan sai dai kyanta ya Kare a banza ba dai tayi aure inda zata huta ba ita da hutu sai dai tayi nata gaji da aiki, duk wani haske na rayuwarta saina dusashe shi Bari ma ki gani". Ta yunkura ta Miki ta nufi bed room dinta tana lalubar wayarta. Ayi hakuri ba editing Naga kwanaki wata na fadar kada a karanta rubutun ba kyau. ✨ ✨ AUREN HUCE HAUSHI ✨ ✨ Story & Written By Maman Fatimah. Godiya da yabo sun tabbata ga Allah s.w.a, salati da daukaka da Amincin su tabbata ga shugaban mu Annabi MUHAMMAD s.a.w.w. Page twenty two. ( 22) 📖🖋️ ________Mahmud Bai bar cikin hotel din ba Saida yayi sallar insha'i, cikin gari ya koma gurin malam lokacin sun Fara karatun dare da maza manya Kamar Yanda suka Saba, shima littafin ya dauko na Riyadussalihinp ya zauna daukar karatun sai gurin takwas, bayan jama'ar sun watse ya rage daga malam din sai Mahmud da Habib. Ganin Mahmud din ya zauna malam yasan da magana, Saida Habib ya gama gyara littatafan kusan aikinsa ne shida Abubakar, bayan fitar Habib din kusa da malam din Mahmud ya matso Yana Fadin Baba barka da dare". Cikin sakin fuska malam ya amsa Masa Yana Fadin. "Ya akayi ka zauna har wannan lokacin baka koma ba kasan ba sabawa tayu ba itama ya kamata a ringa kula". Kai yadan Sosa Yana Fadin in Sha Allah yanzu zan tafi daman na tsaya ne Ina son muyi magana". "To Babu laifi ina saurarenka". Qara sadda Kansa yayi Yana Fadin. "Daman game da maganar tafiyar da zamuyi ne nace ko za'a samu wadda zata zauna da yarinyar Nan ne?". Gyaran murya malam din yayi kafin yace "Eh hakan yayi dai dai saidai ka tuntubeta kaji nata ra'ayin tunda Naga gidan nasu da wadatar juma'a ko wata zata tayata zaman tunda kasan sha'anin yau sai a hankali kada a Kai Mata wadda za'a samu matsala". Tunda baba malam ya fara Kora bayani Mahmud ke gyada Kai sai da ya Kai Aya sannan Mahmud din yace. "haka ne in Sha Allah zan nemi shawarar tata duk yanda mukayi zan fad'a maka, na gode" Ya fada kafin su fad'a wata hirar akan wani sabon project da suka samu daga usaid karshi gwamnatin jihar Bauchi da sukazo musu aikin plane na shekara bakwai. Bashi ya bar gurin malam ba sai wurin Tara da rabi, daya fito ma majalissar su ya nufa gurin su salisu Nan suka dunga yi masa chari akan ya zagaye ya tafi gidansa bai nemi rakiyar kowa ba ko rowar ganin Amarya yake musu, shi kuma ya Kare kansa da hujjar Shima be San da zuwenta ba kawai da yamma Baba malam yace yaje can gidan ya jira Alhaji Jafar Yana son ganinsa, Yana zuwa kuma ya ganshi da zahrar ya kawota da kansa, to wa zaya Kira Kuma ihu bayan hari. Sunyi masa Allah Sanya Alkhairi da Alkawarin zuwa su gaida amarya sai goma ya karbi lifan din Habib ya nufi hayin banki. Lokacin daya shiga falon shiru ba motsin komai sai ni'imtaccen kamshin turarukan wuta 'yan asali da kuma na roomfreshner masu dadin kamshi lumshe ido yayi Yana shakar kamshin.Nan da Nan yaji wata irin kasala ta rufe shi ga wani mahaukacin feeling yana bijiro masa tun bayan barinsa gidan yake fama da wani irin tunanin ta duk motsin da zeyi sai ta fado Masa,moment din yake tunawa duk da ba cikin dadin Rai yayi ba Amma ya tsaya Masa a zuciya sosai Kamar magnet haka ya d'afe Masa. A hankali ya taka zuwa tsakiyar falon komai tsab Kamar wani mahaluki Bai shiga falon ba, harya Fara Hawa steps din da zasu sada shi da bedrooms nasu hankalin sa ya Kai wurin dining din manyan warmers ya gani a hankali ya sauko ya nufi gurin abinci ne mai rai da lafiya sai Kuma pepper soup na cow tail da hadin salad da alama na ba'a taba ba yasan aikin Ammarta ne kada kai yayi Yana fadin "wato abincin ne bazataci ba ko me take nufi? baiwar Allah ta Bata lokacinta ta bada a kawo Amma ba za'aci ba" Dakinta ya nufa Yana zuwa ya kama handle din yaji ta a rufe, shiru yayi wata zuciyar na cewa yayi knocking wata Kuma na kwabarsa, juyawa yayi ya koma gurin dining din shi dai baze iya cin abinci Mai nauyi ba, abincin ya dauka yabar pepper soup da hadin salad din tinda bashi da yawa. Gurin Mai gadi ya nufa yana Fadin "Ga abincin nan a samu ayi amfani dashi yayi yawa". Da hanzari ya taso Yana fadin "To yallabai ai dazu ma Mai gidan ta Aiko dashi har Saida na bawa wasu Yara ma sauran, wannan kuma Bari na kira Mustapha yazo ya kai musu can gida madallah dai an gode da dawainya". "Haba ba komai gashi idan yazo sai ya biya mashin dasu". Ya aje Masa 5k akan warmer din ya juya yabar Mai gadin Yana sheka Masa addu'a da fatan Alkhairi. Saida yayi wanka sannan ya dawo dining din yaci iya Yanda yake ganin ya isheshi sauran ya Kara kaiwa Mai gadin sannan ya koma daki. Kan kujerar desktop computer ya zauna Yana kunnawa da ita akayi masa connecting din CCTV din dake gidan, a hankali ya fara watching Yana kallon duk wani abinda ya faru a gidan wani irin murmushi yakeyi lokacin daya ke kallon dabin su da ita da yadda tasha kukanta, wani Abu daya ja hankalinsa shine yadda yaga su zilai da yadda yaga sahura tayiwa zilai dabara ta turata ciki gurin zahra, ita Kuma tana waya bayan ta gama Kuma yaga ta shiga store ta fito tana kudundune Abu a cikin hijabinta wanda be San ko menene ba, take a Nan ya Dora mata question mark. Saida ya Gama ganin komai Dan yanzu ma littafi ne take karantawa har lokacin daya murda handle din kofar da Yanda ta wani zaro sexy eyes din ta Kamar zasu Fado kasa saboda razana, murmushi yayi Yana fadin "matsoraciya kawai wannan za'a Sha drama da ita Dan Naga alama shagwaba tabi jikinta Bata San wahala". Zahra kuwa tunda ta shige ta rufe kofarta tayi duk abinda zatayi na al'adun kwanciyar ta, sai ta dauko littafin ta du'aul mustajaba tana karanta addu'ar barci, bayan ta Gama ta shafa shiru kawai tayi tana tunane tunanen zuci ba, memories na abinda ya faru tsakanin ta da Mahmud ya shiga dawo Mata, Dan guntun tsaki tayi tasa hannu a kirjinta data wuni suna Mata zugi, a hankali ta Fara magana Kamar Mai gudun kada wani yaji ta. "Jarababbe kamar maye duk ya cinye min labba da harshe ya shafeni tas yana wani gurnani kamar na zaki, da wasu idanunsa da gani na fitinannu ne! Ni Zahra na gamu da gamona na shiga Tara bama uku ba, shikenan na Zama nama sai Yanda hali yayi". Hawaye ne sharrr suka zubo Mata duk lamarin ya cud'e Mata ta rasa mafita, alwala ta shige ta dauro tana ayyana gara ta kaiwa Wanda baya barci wani abu Kuma Bai taba boyuwa ba a gurinsa kukanta tasan shine sami'uddu'a. Sallah tayi raka'a hudu ta zauna tayi istigifari da hailala da salati ga fiyayyan halitta Annabin Rahama Muhammad s.a.w.w har Saida taji zuciyarta ta samu nutsuwa kafin daga karshen ta daga hannuwanta sama tana Fadi cikin raunin murya da Qasqantar da Kai ga Allah s.w.a "Ya Ubangiji Kaine mafi sani ga abinda yake faruwa Dani, wani Abu Bai sameni ba sai da izininka na gode maka a duk halin dana samu kaina a ciki, ka zama gata na,ka lullubeni da bargon Rahamarka, ka suturtani da suturarka, ka rufa min asiri da rufin asirinka, kada ka barni da iyawata ka iya min da iyawarka, Ubangijina ga wannan bawan naka Nan kasan ko waye shi lamarinsa Ubangiji ka sani ba boyayye bane a gurina Idan Yana da wani kaidi kada ka Bari yayi tasiri a kaina Dan isar Annabi MUHAMMAD a gurinka. Ubangiji kajikaina ka duba raunina ka tausaya min kada ka Bari makiya suga wallena ka bani rinjaye a kan dukkan al'amurana". Duka hannuwanta tasa ta rufe fuskarta kamar me shafa addu'a Amma kuka ta saki Mai tsuma zuciya tana ayyana "Wai fa ita Amarya ce wadda ya kamata ace a irin wannan time din ana can ana riritata kamar a hadiyeta dan so da kauna da tarairaya da kulawa. Amman nata da haka yazo Mata, Astagafirullah Ubangiji ka yafe min zunubina daya janyo min irin wannan gararin rayuwar". Ta dauki dogon lokaci tana shashhsheka a haka barci yaci karfinta ta sulale a gurin yayi awon Gaga da ita. Bata farka ba sai kusan biyar da rabi cikin sauri ta tashi tana fadin "subahanallahi!" Da sauri ta nufi toilet tana addu'ar tashi daga barci, a gurguje tayi uzurinta tayi alwala ta fito sallah tayi ta zauna yin Azkar da karatun qur'ani har gurin takwas na safe. Mahmud Bai dawo gida ba daga sallar asuba gurin Sameer ya wuce, so yake yi suyi duk abinda ya kamata a Nan tunda kwaso jiki ya taho, shi yasa jiya yaqi yin komai yayi kwanciyarsa kawai. Ba karamin mamaki Sameer yayi ba ganinsa da yayi a irin wannan lokacin to ai ko lokacin da taye single baya Masa sakko haka. Amma sai gashi shida yake expecting dinsa gurin one-two haka shine ya ganshi haka kamar an koroshi. Cikin zolaya yace "My man ya naga haka ka duba time kuwa? Ka fito kabar 'yar mutane ko dai da matsala ne na fadawa Babanka manya su shiga ciki, sun baka yarinya girma -girma kana neman ka bada musu yaji a ido duk Wanda ya ganka a irin wannan lokacin daya Kamata ace kana can kana Shan kafi tea, ai sai mutane su dauka fanko aka kawo maka, gaskiya ka yiwa Allah ka koma ni zan shigo mu karasa aikin a gidanka daman meke kawo mu Nan? ba bukatar privacy ba? to yanzu muna dashi kaga no need sai munzo Nan Kuma kasan yanzu ba da bane ". Ya fada ba alamar zolayar yanzu, ikon Allah Mahmud ya tsaya yana kallo kafin yace "ka Gama Alhaji muhammadu tunda Naga alamar roll din tsohona kake playing, to Wai Ina ruwanka da harkar Nan Ina cewa Mata dai tawa ce yanda nayi ra'ayi haka zan tafiyar da abina, ai dalilin daya kawoni kenan kazo mu ida duk Wani aikin da zamuyi kaje kayi sallama da malam ka kama gabanka". Ya zauna Yana dauko laptop din Sameer Yana operatin dinta. Kusa dashi Sameer din ya zauna Yana fadin "Allah ya huci zuciyarka angon Zahra da Safnah....." wani kallo Mahmud ya watsa Masa wanda yasa Sameer yayi shiru ba Shiri, shi kansa baisan sanda bakinsa ya furta sunan safna ba ko alama.✨✨ ✨✨ AUREN HUCE HAUSHI ✨✨ ✨✨ Story & Written by Maman Fatimah. 💎 Page twenty three 💎 (2 3) ________Zahra ba ita ta farka b sai gurin bakwai da rabi, sai lokacin ta tuna ta cewa Musaddiq ya fadawa Ammah ta bar kawo abinci zata dafa tunda ba komai take ba, toilet ta fad'a ta Dan sakarwa kanta ruwa Bata jima ba ta fito Riga da Wanda na Pakistan ta saka tayi rolling da gyalen ta saka plat shoes na daki ta nufi falo Amma zuciyar ta tana ta dar- dar kada suyi arangama da Dodon nata, falon ta shigo shiru sai sanyin A/C da daddad'an kamshin da yake ga curtains din duk a sake ga fitilu masu qarancin haske a kunne saiya bada wani irin yanayi Mai saka nutsuwa. Dan waige-waige ta Fara Kamar tana neman wani Abu gurin sai Kuma ta nufi gurin tv ta tsuguna tana hada socket din adapter din tv ta kunna ta kamo tashar Almajid, kokacin sun saka Qira'ar Muhammad Saddiqul minshawi a cikin suratul ISRA'I sai da ta dai daita volume din sannan ta nufi kitchen din a nutse da takunta Wanda da yawa suke ganin yangace da jiji da Kai alhalin ba haka bane naturally haka Allah yayi ta. Kitchen din ta shiga Kusan shigowarta ta uku Kennan, lokar da taga kayayyakin aikin ta bude ta dauko roba mai Dan Fadi ta nufi store ta debo Irish ta fito wanke shi tayi ta fere ta zuba a tukunya ta kunna gas, sai kuma ta dauko kaza guda ta yanka ta wanke ta zuba seasoning da spices ta rufe, ta jona egg boiler ta zuba kwai hudu a ciki. A gefe kuma ta dauko attarugu da Albasa ta yanka kananu ta aje a gefe Irish din ta Fara dubawa taga yayi ta sauke ta zuba a container Mai zurfi tasa fork ta murje ta dora frying pan ta zuba Mai kadan ta saya attarugu da albasar ta zuba a Kan irish din ta zuba magi da curry ta fasa ta yanka dafaffen kwan a ciki sannan ta fasa danye ta zuga ta juya ta aje ta duba kazar itama tayi Nan da Nan ta hada pepper chicken sannan ta jona tanda electric ta Fara zuba hadin Irish din Nan tana soyawa Kamar masa, tana gamawa tayi pepper chicken. Dora ruwa tayi a karamar tunya kafin ya tafasa ta dauko madara ta bude ta diba a wani bowl ta dama sannan ta dama corn flour a cup, jikin kitchen cabinets din ta tsaya tana bin karatun da yake shigowa daga parlour har sun kai suratul D'AHA. Madarar ta zuba taci gaba da tafasa sannan ta zuba corn flour din ta daure da yayi dai dai yanda takeso ta sauke ta Kara Masa condensed milk a cikin ta juye, hadesu tayi a babban tray tayi ta nufi falon, Nan akan dining table ta jero komai sannan ta koma ta dauko sauran tarkacen su cups. Kitchen din ta koma ta gyara gurin tas, sannan ta koma daki wanka ta shiga, tana fitowa ta shafa lotion dinta tayi simple makeup ta saka saka turarikanta na jiki dasu humra Nan da Nan jikinta ya shiga fitar da wani fitinan Nan kanshi, doguwar rigar Dubai Mai kananun stones pink mai duhu ta saka rolling tayi dan Vail din rigar milk colour sai ta fito balarabiyarta sak Dan idan ba kaji tayi maka Hausa ba bazaka taba cewa tasan ko zo da Hausa ba, tayi kyau matuka yarintarta ta fito sosai idan ka kalli fuskarta very cute sai wani annuri take fitarwa. Parlour ta fito gurin dining din ta nufa cikin takunta das das. Tana mamakin Ina ya shiga Dan ko motsinsa babu har yanzu ita kuma bazataje bedroom dinsa ba, idan ya gaji da zaman dakin ya tunda ba yaro bane yunwar cikinsa ta fito dashi. Kunun madarar ta zuba da masar Irish din kwara biyu kawai ta dawo main parlourn ta zauna tana ci tana sauraren karatun, sai da ta gama ta Kai kayan kitchen ta wanke sannan ta dauko Wanda ta zubawa baba Mai gadi ta nufi kofa a hankali take tafiya a cikin harabar gidan iskar bishiyoyin da sauran shuke shuken suna kadawa gwanin sanyi can gurin gate taga baba Mai gadin ya nufa da sauri da alama budewa zeyi.Dan tsayawa tayi daga gefe idonta Yana kan gate din Dan taji dirin mota zata shigo cikin kankanin lokaci motar ta shigo ido cikin ido sukayi da shi shine yake driving din gabanta ne ya bada ras ras Kuma ya kafeta da fitinannun idanunsa cikin gwaninta ya nufi parking lot, Sameer kuwa Kamar wani sakarai haka yake kallon zahrar Yana tsarkake suna Allah a zuciyarsa ya ganta har kusan hudu Amma da alama ganin tsoro yake Mata sai yau yaga zahirin zahrar, da sauri baba Mai gadin ya karaso yana gaisheta ta Mika Masa Dan Karamin basket din ta juya da sauri ta nufi kofar falon har Kamar tana dan sassarfa ta shige ciki, harta wuce idanun Mahmud suna binta Nan da Nan yayi kicin-kicin da fuska daman ga Sameer ya tabo shi ga itama da kalar nata shirmen, cikin zafin nama ya kashe motar ya Kama kofar ze bude Sameer ya kamo hannunsa ya rike Yana girgiza masa Kai kafin ya dungule dayan hannunsa irin na roko din nan yace. "Pls Dan Allah cool your temper kada kaje mata a haka kayi Mata uzuri Batasan Kai ko waye ba, Kuma infact ma laifinka ne ka tafi ka barta a gida har zuwa wannan lokacin Kuma tana ganin hakan da tayi shine dai dai koni nayi supporting dinta hakan shine dai dai ta nuna maka tasan haqqin abinda ka bar mata amana" . A Dan fusace ya kalli Sameer. "Nine na Bata amanarsa da izuninwa ta fito nan wato. ya kalleta yanda yakeso ko? Matata take kaiwa Mai gadi abinci wannan wane irin zubewar aji ne a gurina? Dubi fa yanda ta fito? Ko baka gani ba?" Ya fada yana kallon Sameer. "Ni banga wani Abu na rashin kyautatawa ba a shigarta, kawai dai idonka wani Abu ya nuna maka na daban gaskiya". Hannunsa ya zare daga cikin na Sameer din ya bude kofar a hankali ba Kamar dazu ba zagayowa Sameer yayi ya rufe motar yabi bayansa Dan Idan ya Bari ya shige irin na jiya ze masa ya ajeshi a waje, kofar ya bude wani sanyi da kanshin girki Dana turarikan daki sukayiwa Sameer sallama Bata Nan sai tv a kunne ana karatun har lokacin. Direct gurin dining Sameer ya wuce yana fadin Bari na Fara da Nan Idan na gama ma gaisa tunda ba bako nake ba ya Fara budewa Yana kallon Mahmud Yana fadin. "Tab da alama Allah ya tarfawa garinki nono irin wannan delicious". Gaba Mahmud yayi Bai tanka Masa ba ya shige ciki. Kofar bedroom dinta ya kalla har dariya take bashi bilhaqqi da gaske tsoransa takeji bare Kuma da jiya ya Dan motsa mata Jamiyya. Ta Dan Dade a bedroom din nata daga baya ta bawa kanta kwarin Gwiwar ta fita ko banza bazata bada kofar da wani na waje ze gane da 'yar tsama a tsakaninsu ba Kar a Raina Mata wayo, fuskarta ta Dan Kara shafawa powder kadan ta Dan Kara fesa mouth freshner Mai kamshi apricot ta nufi kofa tana budewa saura kadan yau ma suyi karon, da sauri taja Baya. Shigar kananun Kaya yayi as usual dan zaman da sukayi ta fashimci kamat ya samu wani freedom ne na sakewa, trouser black da milk T-shirt ne a jikinsa hannunsa daure da agogo sai waya a hannunsa. Baya tayi da sauri tana Dan zare idanu Dan ba Karamin tsoro taji ba, Shima kallon ta yake Kamar ya rungumota ko yaji relief na abinda yakeji a zuciyarsa, amma sai ya share ya Mika hannunsa ya kamo nata ya natso da ita kusa dashi Sosai Yana Fadin "kin tashi lfy?". Ya shafi gefen fuskantar, cikin siririyar murya tace masa "Ina kwana? Shiru yayi Kamar beji ta ba, ya janyo ta suka Fara tafiya a cikin corridorn, sai da suka Fara gangara steps din taji yace waya Baki izinin fita gurin watchman din can?" Ya Dan matse hannunta dake cikin nasa. "Wash!!! Allah ta fad'a ba tare data shirya ba. Dan da gaske matsewar ta shigeta dago Kai tayi cikin narke fuska Kamar zatayi kuka dai dai lokacin Sameer ya dago Kansa daga daddana wayar da yakeyi Jin maganarta Sam beji tahowarsu ba wani irin perfect match couples ya gani sun masifar dacewa da juna ya Dade bega ma'auratan da suka burge shi kamar su ba, a zuciyarsa yake Fadin. "Masha Allah". Zahrar Tace masa. "Ba kowa, Dan Allah ka sakar min hannu wlh zafi...." Ta fada cikin shagwabar da Bata San tayi ba. Murmushi Sameer yake ta saki daga inda yake Dan ba karya yasan muhmud yayi dacen da Basu zata ba abun kamar a film yake ganinsa. Dan lokacin da suka Fara ganinta da Kuma furucin da shi Mahmud din yayi ashe Allah ya karbi addu'ar. Dan gyaran murya Sameer yayi Yana kallon Mahmud din tare da fadar. "Yallabai a bar madam ta karaso mu gaisa Mana ni ba mazauni babe gaba nayi daga Nan" Ya fada da sigar zolaya duk yaga har yanzu kamar Yana Jin zafinsa tun maganar da yayi masa na Safnah. Sassauta rikon hannaun yayi suka ida gangarowa directly dining area ya nufa yana zuwa ya ja Mata kujera ya zaunar da ita sannan Shima ya janyo ya zauna. Gurinsu Sameer ya karaso daga inda yake zaune Yana fadin. "Madam barka da Asuba kingan ni sai yau ki?". Ya fad'a yana Zama kusa da Mahmud. A kunyace ta amsa da "lfy kalau Ya Sameer ya kaje gida? Ina madam?" "Komai lfy ya hakuri damu?". 'yar dariya tayi kafin ta Mike ta Fara bude abincin Wani daddad'an kamshin ne ya doki hancin Mahmud har Saida ya lumshe idonsa, Dan kallonsa tayi sannan ta kalli Sameer tace "me za'a zuba?". Kai Sameer ya girgaiza Yana fadin "ai ni na riga ku ci tun shigowarmu naji bazan iya jiran masu gidan ba saina shide Ina jin kamshin delicious Amma ace saina jira". Ya fad'a Yana dariya.Dan murmushi Mahmud din yayi. "Wato ko Ina saika nuna halinka ko?". "Pls zuba min kawai". Kallonsa tayi kasa-kasa, tace "Toh" Masar dankwalin turawan ta zuba sannan ta zuba pepper chicken din ta tura Masa sannan ta zuba kunun Madarar sannan ta koma ta zauna a darare. Wani cup din ya zuba kunun Madarar ya dauko da fork ya matso kusa da ita da plates din abincin yace. "Oya saka hannu muci". Ya wani hade gabas da yamma alamun ba wargi Kai ta shiga girgaizawa alamar ta koshi Shima ture abincin yayi Yana duban Sameer. "Muje kawai" Ya fad'a yan Jan kujerar baya. "Zanci". Ta fada a gajarce. Komawa yayi ya zauna Yana fadin "fine tunda zakiçi gara Idan mutuwar zamuyi mu mutu tare Dan naga abinda Mata suke yayi kenan Idan aka Basu Wanda ba shine zabinsu ba su kashe shi su auri wanda sukeso". Tunda ya Fara Kora bayani Zahra tayi masa kur da ido tana Mai maita. Kai Sameer ya shiga girgaizawa Yana mamakin wani sabon hali da Mahmud din ya tsira, yaga alama nema yake ta Hana yarinyar Nan sakat. Ita Kuma tunda ta furta zanci Bata Kara tofa ko kalma daya ba, sai kawai ta dauki fork ta cako Irish din ta Kai bakinta ta tauna ta hadiye, pepper chicken din ta dauka taci ta dauki kunun Madarar ma ta Sha duk Yana kallon ta shi kuwa Sameer Yi yayi Kamar Allah Bai halicce shi a gurina ba. Tana gamawa ta tura kujerar da take Kai baya sannan ta dubi shi ido cikin ido tace. "Gashi naci idan kana tunanin zan zuba maka poison a abinci kayi kuskure lalacewar tawa Bata Kai haka ba, Idan na kasheka wace riba zanci? wato ka tafi lahira free ko? duk lodin zunuban daka dauka niga sakarai na lodawa kaina, to Bari na fad'a maka ba saina aikata zunubi irin haka zan rabu da Kai ba A'a salin alin kowa ze kama gabansa ni da Kai tunda daman masu iya magana na cewa tsintacciyar magen Bata mage nasan komai Daren dadewa zaka koma inda ka fito". Ta fad'a Tana wurga masa harara ta wuce ta kyalesu batabi ko takan Sameer da yake fadin "Allah ya huci zuciyar amaryarmu". Da ido Mahmud yabi Zahra har ta bacewa ganinsa "Wai shi yarinya kamar wannan zata saka shi gaba ta fada Masa son ranta amma yayi shiru Yana kallon ta". Sameer ne ya katse Masa tunanin da yake. "Dan Allah kada ka koya matsa tsiwa wlh da gani Bata Saba ba, bakaga jikinta har rawa-rawa yake ba". Ya fad'a Yana kallonsa. "Jikinta na rawa kenan Kare mata kallo kayi har kaga jikinta na rawa ni ban gani ba?". "Subhanallahi! Wace irin magana ce haka wlh ba haka nake nufi ba, Bari naje kawai sai munyi waya". Ya Mike Yana aje rafar dari biyar guda biyu Yana fadin "A bawa madam ace Mata na wuce tunda ka Hana muyi sallama". Ya biya Kan center table ya dauki keys dinsa yayi gaba tunda yasan ba magana Mahmud ze Masa ba Dan da gaske yazo wuya yanda yanayin fuskarsa ta nuna. Bayan fitar Sameer, Mahmud kasa ko motsin kirki yayi wai shine tsintacciyar magen? Da gasken gaske maganar ta dokeshi kwafa yayi Yana fadin zakiga tsintacciyar mage iya ganinki sai kin gane bakin rijiya ba gurin wasan makaho babe". Ji yayi kwata kwata abincin ya fice masa raga Rai duk yanda yake jin yunwa ture abincin yayi ya Mike ya nufi bedroom dinsa Bai jima ba ya fito cikin shigar yari filtex fari dinkin boda da farar hula a Kansa Yana baza qamshinsa na Ibada, yayi waje. Tunda Zahra ta Fadi maganar dake ranta taji zuciyarta wasai, gefen bed dinta ta zauna tana mita. "Haka kawai saika wani ringa sakarmin magana ba control duk abinda yazo bakinka saika fad'a mini, Wai na saka wani Abu girkinma ba saina Kara yo da Kai ba sannan na Zama suspect daman saboda A kashedin Ammah ne yasa nayi, kwana biyu amma kamar na shekara duk ka matsa min ka karbe min waya nayi Shiru na Zuba maka ido Naga gudun ruwanka, na fita mikawa bawan Allan Nan abinci kace da izininwa? Haka kawai ka zamar min karfen kafa". Ta fad'a Tana kwafa. Tunda gari ya waye Ammah Bata zauna ba shirye-shiryen tafiyar Inna maimuna take wadda zata tafi yau, cikin Shirin fita unguwa Mama ta shigo lokacin Ammar na zubawa innar kilishin da Abba yasa akayi Mata zaunawa tayi tana Fadin "Inna yau zakiyi Mana ta Baki wlh ba dadi". "Kayya Hajiya Rabi banda abun yazo da sammazi Aida na jima da tafiya gida daga zuwa biki na share our na zauna kinsan da Ardo Yana Raye hakan ba zata faru ba yaushe ze Bari". "Haka ne Kam Allah yayi musu Rahama". "Amin" su Inna suka amsa. Leda mamar ta aje kusa da innar tana Fadin. "Gashi Inna ba yawa Allah ya kiyaye hanya ni fita zanyi unguwa nasan kafin na dawo kin tafi". Gdy innar da Ammah sukayi Mata ta tashi tana yiwa innar fatan sauka lafiya. Sai bayan ta wuce ne innar ke tambayar Ammah ina Hameeda ne Naga tun she jiya da safe bata qara ganinta ba. "Jiya kina barci tazo Nan Wai ta tafi Jos gurin yayar mamansu larai". "To ba laifi hakan ba laifi daman shekaranjiya ne da dare na fita zanje can inda na baza ganyen yandi Dana shanya naji uwar tana surfa Mata zagi ban dai San dalili ba Amma naji ita yayar tata tana Fadin sai kije kiba Zahra hakuri Mana tunda kanwar uwarta ce ni dai Nan na barsu Dana dauko shanya ta". "Allah ya rufa asiri kowa yayi nagari Kansa ya yiwa kuma sharri Dan aike ne duk inda ka tura shi ze dawo, bansan abinda yarinyar Nan ta tsare musu ba, bana raba day biyu da abinda sukasa Hameedar tayi inaga daga baya ta gane Bata kyauta ba shine tayi magana uwar ke zaginta". Sun Dade suna tattaunawa. Gurin Sha Sha daya da rabi magaji yazo ya dauki Inna maimunar zuwa gidan Zahra. Zahra na barci Dan batasan lokacin da barci yayi awon gaba da ita ba, cikin barcin taji alamar bell din kofa ta yunkura ta tashi ta yafa Veil din rigar saman gashinta. Tana budewa taga Inna maimuna da magaji, jikin innar ta fada kawai sai ta saki kuka Wanda ita kanta bata San kona menene ba. " Ke matsa can da Baki rabuwa da shiririta saboda Allah menene abin kuka magidanciya dake, Dan Allah duba min Nan Mai sunan malam wannan ai rashin wayo ne koba haka ba?" Ta fad'a Tana kallon magaji, duriya yayi Yana fadin "kumfi kusa Inna na bankwana ne tunda Idan Kika shige wannan lungun Sai baba ta gani, ni Naga ma kinyi Rana gaskiya har yanzu Baki tafi ba". "Ai a Gombe zanyi kwana biyu gidan Dan aminiyata da nayi rainonsa to nayi Masa Alkawarin zuwa idan zan tafi". Ita dai Zahra tunda ta kwantar da kanta a cinyar Inna maimuna Bata Kara dagowa ba, jinta a jikin innar sai takejin wani sauki da nutsuwa suna saukar mata. Gashin Kanta innar ta Dan shafa inda gashin ya fito tana Fadin shi dai wannan gashin baisan kitso ba Kullum Yana Nan a nannade kamar gammo". Dan turo Baki tayi tana Fadin "Ya zanyi kinsan ba kitsuwa yake ba ko anyi idan ya Dade kwana biyu ne kawai ga zafi". "Allah ya kyauta kawai dai 'ya'yan zamani Amma har yaushe za'a yita Zama da Kai haka? Yau Wai uwar taku tace meya samu wayarki ko an Kira Bata shiga? tasan ba rashin caji bane tunda ance Kuna da wannan abar Mai amfani da hasken Rana" Dan Jim Zahra tayi tace ya karbe wayar ai hakan be dace ba, Sai kawai tace. "Nima bansan meye matsalar ba kawai rufewa tayi taqi kunnuwa". Magaji ne Wanda yaketa faman cakular waya dago Yana fadin dauko mugani ko abun minor ne". "Bata gurina tana gurinsa ban sani ba ko dubawa ze bada ayi". "Shu wa?" Ya fad'a da sigar zolaya, banza tayi masa kamar bataji ba. Tashi daga jikin innar Zahra tayi tana Fadin Bari na dawo wlh murnar ganinki ta mantar Dani ko ruwa ban kawo Miki ba". Tayi gaba innar na Fadin "dawo Zahra'u nida ba bakuwa ba". Gaba tayi abunta. Saida ta ciko tray babba da dangin Zaki da sanyi har sauran pepper chicken din ta zubo musu, tunda ta aje innar ke binta da kallo tana jinjina abin wannan cimakar bata mai Karamin kafin bace ko ance gida tallafin qungiya ya samu har abinci ci susuka dauki nauyin bashi?" Ita dai shiru tayi Bata tofa ba Amma a kasan zuciyarta da maganganu fal Wanda zasu tattaunawa da 'yarta. Ware ciki magaji yayi ya kwashi gara har Inna na Masa Dan biki. Wayarsa Zahra ta barba ta Kira Ammah ta gaisheta itama abinda ta fadawa innar ta fada Mata game da wayar lokacin data sauke wayar harda share 'yan hawayenta, magaji Yana Mata tsiyar shatwabarta tayi yawa ita Batasan ta kusa Zama uwa ba,Inna na Taya shi. Sai da Innar ta Gama sannan ta tambayi Zahra. "Wai Ina Mai gidan nawa ne banji motsinsa ba tunda nazo?" Kafin Zahra ta lalubo abin fad'a magaji ya rigata Yana fadin. "Ai kin baroshi can a unguwar mu gashi nan suna magana da Ya Abdul Hakeem a kusa da masallaci har suka daga Mana hannu". "Awoh to ai kasan ban waye dashi ba sai a hankali". Nasiha Sosai da ban baki Inna maimuna ta Kara yiwa Zahra tare da kara jaddada Mata mashinmancin biyayya ga miji. Kaya Zahra ta zubawa inna a wata babbar leda harda atamfa dasu turaruka taba Magajin ya rike mata. ****** Tafiya ce miqqqqiya daga Azare zuwa Babban mutum ta Babura jihar jigawa, direban daya dauko Mama da Asabe ya Dan juyo yana kallon Asabe wadda ta maida hankali gurin cin doyarta da kwai da suka saya a kanya babba yace ",munzo Babban mutum fa Ina zamuyi kinyi shiru alhalin kece idona tunda wannan ba yanyata bace". "To na manta wallahi kasan da Dan Habu muke zuwa na zata shine ita dai Mama Bata cewa komai Dan niqab nema a fuskarta badan ta matsu da son ganin malam na bande din ba da ba yanda za'ayi tayi wannan kasadar Dan yanda ta fadawa Abban Itas/gadau zasu wata dubiya Alhajin yaso Bala direba ya Kaita ta nuna Masa da kawarta matar tshon Ambassador zasuyi tafiyar abinda ya Hana Bala direba kaita kenan, hanyar tinkin ta nuna Masa alamar Niger zasu shiga. "Yanzu ke Asabe a she Niger zamu shiga shi ne kikace min kauyen Babban mutum wlh da bani da takardar ecowas da Saida na zubeku ku nemi wadda zata karasa daku kinsan kuwa yanda suke da doka da order?". Tafiya ce miqqqqiya daga Babban mutum zuwa bande, sun Sami tarba Mai kyau daga yaran malam na ciki suna fitowa su Asabe suka shiga malam din yana zaune akan buzu da wani zabgegen carbi a hannunsa ya amsa musu sallamar su suka zauna suna gaishe shi. Asabe ya dago kai kalla. "Baki fad'awa Hajiya sakona ba?" "Allah ya taimaki malam na fad'a Mata cewa tayi na kawota gurinka tazo taji Koda yanda za'ayi lamuran ne suke neman canza fasali". Carbinsa ya Fara ja yana girgiza Kai yayi hakan kusan say uku kafi ya sauke wani dogon numfashi yana Kara girgiza Kai. Mama cikin kidimewa ta furta. "Da matsala ko malam?". "To da matsalar Amma Abu mafi ban mamaki shi yaron har yanzu bana ganin komai akan Lamarinsa kwata-kwata sai yau Naga wasu mutane a Kan lamarinsa da Kuma itama yarinyar an tasa ta gaba da dafa'i shiri Kuma na gasken gaske sai dai naga wata tafiya a gaban mijin nata da alama Kuma tafiyar da Alkhairi q a cikinta sai dai idan dauke hankalinsa za'ayi daga garin kwata kwata, idan ya tafi ya kasa ko tunanin garin bare ya dawo, idan ba haka akayi musu ba ba makawa sai kin Zama 'yar kallo a gidan dan duk yaran gidan Mata ba wadda tauraruwarta ta kama kafar tata da gaske haka Allah ya yita da madaukakin Alkhairi". Zuru Mana tayi ta kasa magana, maganar dai ita kenan Zahra tafi nata 'ya'yan. "Malam ayi duk abinda ya Kanata inda hali ma ya rattaba Mata saki kafin yabar garin". ""Abinda ban gani ba kenan a cikin auren nasu Dan Idan shi ne ze saketa to inaga sai dai ta mutu da auren Dan Banga hakan ba a tare dashi,ni a yanda na gani a istiharata ma ya Santa batun a Nan garin naku ba Kuma da soyayyar ta Mai karfi a zuciyarsa wadda har abada baze iya rabuwa da ita ba, ayi dai hakan yanda Idan iyayenta suka gaji da jiran dawowarsa Bai dawo ba su raba auren da Kansu". Bayanin ya kwantawa da Mama hankali, ya kawo abubuwa ya bata har Wanda za'a hada da tuaren wuta a bawa zahrar Idan harta turara Mahmud ya shaqa shida Azare har abada. Kudi masu kauri Mama t✨✨ ✨✨ 💎 AUREN HUCE HAUSHI 💎 ✨✨ ✨✨ MAMAN FATEEMAH PAGE TWENTY FOUR (24) _____ Tun bayan tafiyarsu Inna da magaji sai gidan ya zamar Mata shiru Bata Dade a parlourn ba ta koma ciki, da taga tunani yana neman ya dameta saita dauko qur'an dinta ta Fara karatu Saida taji Kiran sallah ta aje taje tayo alwala. Bayan ta gama sallar ta Haye gado ta Kara A/C tayi kwanciyar ta ba tafi minti talatin da kewnciya ba taji alamar Baki ana Danna bell, tashi tayi ta nufi kofar da gaske dai bazata samu barcin na kirki ba,Kofar ta bude a hankali su Amatu ita da Aunty safiyya ne guri daya suka zauna a Dr sulaimanu Adamu model school of Hygiene inda tayi service, su Kuma permanent lecturers, rabon ta da Amatu tun ranar daurin aurenta dan lokacin da zata wuce jama'are garinsu Bata biyo ta gidan Ammah ba daga gidan Aunty Hasana ta wuce kawai. Cikin nuna tsantsar farin ciki Zahra ta rike hannun Amatu tana fadin "wlh nayi fushi Amah Ina nan Ina jama'are? Amma kikaqi dawowa ni Aunty safiyya zanyi welcoming kawai Amma ke kam dai sai a hankali kawai, Aunty sannu da zuwa". Ta fad'a Tana Basu hanya tare da karbar yaron Aunty safiyya dake hannun Amatun. "Hakan ma na gode tunda an karbi Auntyn ai shike nan tunda ita ta gari batayi laifi ba saini da nake can kauyen mu". Ta fad'a Tana Zama a cikin one seat dake kusa da ita. "Eh wlh Aunty tana da excuse a gurina tunda nasan Bata Nan taje gida sokoto Amma ke kuwa ko waya fa Baki Kira kinji ya ake ciki ba". "Kice dai ban Kira ba. Amma tambayi Sajida kiji na kirata yafi sau ashirin ma ke dince lokacin Kiran baze yuwu ba Sai ki qara narkewa". Dariya suka saka su duka harda Aunty safiyyar. "Wlh Amah saina rama kinci bashi, Wai na narke kamar wani danyan tuwo". "To da mecece? mutuniyar dake somewa Kikayi fa dif kika dauke wuta". Kyale Amatu Zahra tayi ta karasa kusa da Aunty safiyya ta zauna ta Dora Shureem a Kan cinyarta tana Fadin. "Aunty sannu da zuwa Ina yini?" "Lafiya kalau Amarya ya Amarcin Naga ya barbeki kanwata Masha Allah". Dan sinne Kai tayi tana Fadin "Kai Aunty Ina wani Amarci a Nan kawai dai". "Gulmammiya Kinga yanda kikayi wani mahaukacin kyau kuwa? Ai da gani Amarci ya tabbata a gare ki,wa Zaki kife a baibai yarinya Kar nake kallonki fa". "Allah ya shiryeki tunda haka Kika zama, Bari ki gani". Ta Mike da Shureem a hannunta ta nufi kitchen, saida ta Zuba musu kayan garar a plate ta dauko musu ruwa da drinks ta dauko plate ta fito tana Fadin "Amah shiga ki dauko dayan Dan Allah". Sai da suka Gama sannan Zahra tace su shiga suga gidan, ko Ina suka shiga Fadi suke Masha Allah! a gurin fridge din dake cikin Dan Arc din dake tsakanin kitchen da dining area ne Aunty safiyya ta kasa hakuri Saida ta magantu lokacin data Kai hannu ta bude tana fadar. "Yau ne ganina na biyu da fridge din nan naso shi kamar qaddara Amma da aka fad'a Mana kudinsa Saida na Raina kaina" "Kai haba Aunty bakiyi niyyar saye bane". Zahra ta fada. 'yar dariya Auntyn tayi. "Bazaki gane ba Idan ci baizo daya ba ai koshi ma baya zuwa daya". "Haka ne kam Aunty". Amatu ta fada, suka nufi bedrooms dinta ko Ina dai maganar daya ce Masha. Amatu ce ke fadar "Allah ya mayar damu danshinki". "Amin. Amma Banda kalubale irin nawa, ba Dadi Amah har gobe abun Yana damuna bani da nutsuwa ko Kankani wlh duk lamurana sun tsaya cak bani da wani karsashi irin na amarya a gidanta, komai ganinsa nake Wai banbarakwai kamar a mafarki haka". Sai Kuma idanunta ya ciko da hawayen da taketa kokarin kada su zubo. "Ayya haba Zahra kiyi hakuri Mana, ai zuwa yanzu yaci ace kin hakura da koke-koken Nan tunda Mai abkuwa ta abku ai sai hakuri ki rungumi abinda Allah ya Baki ki dangana wata Rana sai labari". Aunty safiyya ta fad'a. Parlour suka dawo sukaci gaba da Hira, rabi duk ban Baki ne Aunty safiyyar kewa Zahra da nuna Mata ribar hakuri a cikin hirar ne Amatu take fadawa Zahra sakon Sajida na tana kiran wayata Amma Koda yaushe switch off. Dan lumshe ido tayi sannan ta bude tana kallon Amatun. "Matsala wayar ta samu shi yasa ba'a samuna Amma in Sha Allah soon zan sayi wata, yanzu bani taki na kirata". Wayar Amah ta Mika Mata tana dialing din number ta. Tana dauka ta Fara mata tsugudidi. "Yau wacce Rana Amatu ta kirani". "Assalamu Alaikum ayi sallama Mana bestie". Ta fad'a tana murmushi. "Kai!!! wa nakeji haka bestie, haba Dan Allah kin kyauta kenan ba waya ba wasika kin barni a tunani kala-kala Sam na kasa samun nutsuwa". Tashi Zahra tayi ta shige ciki tana Fadin "Bari kawai bestie guy din nan ya fa karbe wayar tun ranar da Kika tafi ya dauketa da safe daya shigo, shine fa daya shigo ya tarar duk na hargitse gado ina neman ta yace tana gurinsa, ya kama min wasu zantika akan Kiran da Musbahu yayi ranar ni kuma na kasa hakuri shine yayi min Rashin mutunci Kuma ya hanani wayar". Ta fada kamar zata fashe Mata da kuka, tambayar ta tayi yanda abun ya faru Bata rufe Mata komai ba ta fada Mata. Bata katse Mata hanzari ba har ta gama. "Amma ban taba sanin Baki da wayo ba sai yau, Gaskiya Baki kyauta ba ko alama Ina hankalinki ya tafi kada ki Kara Koda Wasa saboda wani ki ciwa mijin aurenki fuska ai wallahi jarimi ne daya iya hadiye fushinsa bakiji a jikinki ba". Ta fada a kufule, kit ta kashe Kiran. Ajiyar zuciya Zahra ta sauke tana kallon wayar a zuciyarta tana fadin ji a jiki na nawa Kuma ba ze fadu bane shi yasa. Lokacin da zahrar ta fito wasu bakin ta tarar sun shigo su biyu har Amatu ta kawo musu ruwa da drinks suna hira dasu Aunty safiyya, sallama tayi musu sannan suka gaisa Nan Amatu tace musu "ga matar gidan nan". "Masha Allah" Suka fada a tare sannan babbar wadda zatayi kamar sa'ar Aunty safiyya tace "mune makotanki da hannun dama sunana Hafsat Amma ana kirana maman junior, wannan Kuma kanwata ce Nuratu da take karatu a Nan Abubakar Tatari Ali polytechnic (ATAP) aiki ne ya kawo Mai gidana mu 'yan Taraba ne". "Masha Allah! Allah ya taimaka ya bada sa'a". Suka fada. Sun Dan jima ana hira dasu sannan suka tafi har gate Amatu ta rakasu da ledar kayan garar biki. Suma mikewa Aunty safiyya tana goya Shureem da yayi barci, Dan langabar da Kai Zahra. "Wai har zaku wuce ne Kuma Aunty?". "Eh mana zan shiga gidan fachalata data haihu bana Nan". "Amman Banda ke dai Amah gaskiya tunda nasan kina garin Nan sai karshen wata keda jama'are". Aunty safiyya ce ta tari numfashin zahra "Ai ita ke driving dinmu ya zan barta a Nan ta dawo Miki special ko weekend ne". Alamar bude kofar da akayi ne yaja hankalinsu, Mahmud ne ya shigo Yana musu sallama da katuwar leda a hannunsa, tunda ya shigo Aunty safiyya ke kallonsa ita dai tasan wannan fuskar amma ta Yaya za'ayi haka ko Kuma kama ce kawai. A cikin takunsa na cikakken namiji ya shigo, da sauri Zahra ta nufo gurinsa tana Fadin. "Sannu da zuwa". Tana Mika hannu zata karbi ledar. "Da nauyi bazaki iya dauka ba". Ya fada Yana kallon ta. Har cikin kitchen ya shiga da ita sannan ya wuce bedroom. Amatu ce ta zunguri zahra. "Ke! meye hakan Kuma? Kika wani sharesa Kada dai kice min sokoncin da kike bazawa a gidan kenan ko Kuma Dan kin gammu ne kikayi wani biris dashi". "Gaskiya Kam ki dage ki Kama mijinki irinsu tsada suke". Aunty safiyya ta fada tana nunawa Zahra hanyar daya bi. "Kai! Aunty Kuma ......" Bata karasa ba Amatu ta Kama hannunta ta nufi steps din tana Fadin "kije kawai tunda daman tafiya zamuyi saina shigo Saturday in Sha Allah". Dan raurau tayi tana kallon Aunty safiyyar. "Na gode Aunty ku gaida gida saina zo har gida ban gajiya". Dariya Auntyn tayi. 'Haba dai sai dai mun dawo, wannan turaren kada kiyi Wasa dashi tun daga besse na taho Miki dashi kakata ta wurin Babana take haduwa da Kanta Yana da matukar kyau sosai ba sai fada Miki ba da kanki Zaki nema". Dawowa tayi Saida ta rakasu har gurin mota duk da mitar da Amatu ke mata, ta hadasu da kayan garar fal ledoji biyu dasu bokitan roba da mug masu kyau da plates Wanda Aunty Hasana ta bada aka kawo mata saboda Baki masu zuwa. Saida suka fice daga gidan sannan ta dawo ciki. Bata shiga ciki ba a parlourn ta zauna tana mitar. "Idan na shiga me zan Masa wanda yake ganina a wata Mai neman rayuwarsa". *** Saida Amatu ta dai daita a titi sannan da Dan dubi gurin da Aunty safiyyar ke zaune tana rungume da Shureem. "Aunty nifa wani Abu ya bani mamaki da daure Kai" "Kamar me fa?". "Duk gari ya dauka an aurawa zahra Almajiri k'olo saboda ita ba 'yar Alhajin bace, surutu dai gashi nan, ni Kuma yanzu Naga sabanin abinda ake fada, yaushe Zaki kalli wannan kice Yana Qasqantacciyar rayuwa irin wadda ake fada?". "Ni Nama fiki mamaki Dan ni dai Idan ba gizo idona yayi min ba ko Kuma kama ce ta halitta tunda ance kowa Yana da Mai Kama dashi a wani gurin, da sai nace Miki M.M DANGE na gani". "Waye hakan?". Amatu ta tambaya. "Bazaki gane ba Amatu wasu Family ne a sokoto masu mahaukanta kudi Nima fa sau daya na taba ganin M.M DANGEN a bikin wata cussing Dina zainab data auri Dan Family din, Kai gaskiya bashi bane inaga Kama ce kawai, amma Kuma kamar harta baci sai dai ba yanda za'ayi DANGE ya iya rayuwa a nan". "Kamar Yaya Aunty?" "Tab kinsan kuwa waye shi? ai inaga kaf ba Wanda ya mallaki abunda ya mallaka a duk Family din, gashi yaro matashi Kinga gidansa na sokoto ma kuwa? Banda na Abuja da sauran garuruwa, to in kuwa shine me zeyi da Dan wannan gidan ai ji zeyi kamar Yana rayuwa a kurkuku ne, bama shi bane shifa ko bodyguard dinsa abin kallon ne Suma sun Zama done fa" Ido Amatu ta zaro. "Kikace wannan gidan kamar kurkuku? Duk yanda na ganshi Aljannar duniya". "Naki wasane Amatu. Allah ya kawo dalilin da Zaki shiga ko gidan daya daga cikin families din DANGE ne kiyo kallon duniya me Kika gani a Nan kedai Allah ya Kai damo ga garawa kawai, Dan dai a wannan zuwan da nayi sokoto naje yiwa zainab din barka naji wasu a cikin family din sunata hirar MM DANGEN Wai ko ya bar kasar ya koma turai tun bayan samun wata matsala Mai zafi a cikin family din wadda ta tada kura har rayuka suka baci". Da ire-iren hirarrakin suka karasa gidan barkar. ... Tana zaune a Nan parlourn ya fito cikin kananun kaya da karamar leda a hannunsa direct inda take ya nufo ji tayi gabanta ya Fadi. "Ya Ilahiy" ta fada a zuciyarta. Gefenta ya zauna Yana Fadin "Wash!! I am tired wlh samo min ruwa Mai dan sanyi". Yayi maganar yana dan matsowa jikinta. Da sauri ta tashi yabi ta da kallo Yana kissima abubuwa da yawa a kanta kunyar ta tayi yawa yasan sai yasha fama kafin ya rabata da ita yanzu dai most important thing ya samu shakuwa da ita sosai. Ruwan da farm fresh yogurt da snacks ta bawo Masa, idonsa a limshe Kamar me barci Amma Yana kallon ta yanda take tafiya kamar me counting steps sai rausaya take. Table coffee ta janyo ta Dora tare da bude Masa ruwan ta Zuba duk Yana kallonta. Ajewa tayi ta juya zata wuce taji hannuwan mutum duka biyun ya zagaye k'ugunta ya mannata a jikinsa ta baya, yayi Mata bazata Dan ko motsin mikewarsa bataji ba ko alama, a tare suka sauke ajiyar zuciya juyota yayi gabadayan ta suna facing din juna Yana Mata wani duban kasa-kasa. Narke fuska tayi Kamar zatayi kuka tace Masa. "Menene Kuma? gafa ruwan Nan na kawo maka". Fuskarsa ya matso da ita dai-dai tata yace. "Haka ake tarbar miji? Ki bani abincin yunwa nakeji fa, tun safe banci komai ba tunda kika tada min hankali abincin ya fice min daga Rai, waini Kika kalli kwayar idona Kika gasa min maganganu son ranki ko?". "Ni me nace, cewa fa kayi zanyi poison dinka ni banji haushi ba sai kai, kisa fa? To me kayi min, ni na daina abincin ma ba shike nan ba ban dafa ba bare na zuba maka guba". Ta fada tana kokarin zame jikinta, Kara gyara rikon da yayi Mata yayi ya nufi two seat da ita a jikinsa kan cinyarsa yayi Mata masauki, ya Kai hannunsa daya ya zame veil din da tayi rolling gashin ya shiga shafawa yana fadin. "Nifa da Wasa nake Miki dazun bada niyyar na bata Miki rai ba na fada, so I am very sorry Baby in Sha Allah bazan Kara fada ba, na Saba haka nake yiwa kakata Hajiya Inna a irin wannan lokacin na break shine na tunata da ita na fada Miki kema Ashe lefi zanyi, yanzu muje na tayaki ki Samar Mana light Abu muci bana son cin Abu Mai nauyi sosai da dare nasan kafin mu Gama anyi magariba ko" Ita dai tayi tsumu tsumu duk ta takura fatan ta ya saketa ta fece tunda Allah yasa yanzu ba 'yan tabe taben bane a Kansa a iya gashi kawai aka tsaya. Dagota yayi daga jikinsa ya rike hannunta kamar wata 'yar baby suka nufi kitchen, ledar daya shigo da ita ya dauko ya Dora a Kan cabinet din kitchen din Yana Fadin "zo ki cire wadan Nan daga ciki. Kayayyakin amfanin gida ne masu yawa harda su biscuits su chocolate, sai da ta saka komai a muhallinsa sannan ta Fara hada abinda zatayi, kujerar kitchen ya samu ya zauna Yana kallon movement dinta friend spaghetti Mai vegetables tayi sai tayi gasmeat. Lokacin data Gama komai an Fara Kiran sallah. Tare suka fito ya mannata da jikinsa a haka ya nufi bedroom dinsa da ita suna shiga ya zaunar da ita Kan sofa ya wuce toilet. Sai daya rufe kofar sannan ta tashi ta wuce nata dakin wanka take sonyi. Koda ya fito Bai ganta ba beyi mamaki ba yasan za'ayi haka, lokacin daya leka ya fada Mata ya wuce masallaci tana toilet. Saida yayi insha'i sannan ya shigo gidan abincin Mai gadi ya dauko ya futa ya Mika masa, daya dawo be nemeta ba,sport news ya kamo yana kallon labarun wasannin da akayi Bai gani ba. Zahra Kuma da tayi sallah saita zauna tayi Azkar na yamma da Bata samu tayi ba, data Gama tayi shafa ta saka riga da siket English waars combination din milk da maroon tayi rolling da milk veil tayi kyau kamar ka dauke ka boye body mist kawai tayi amfani dasu kusan kala uku cikin Wanda ta gani a cikin locker din mirror dinta sai kamshin ya Bata wani irin Dadi Mai kwantar da zuciyar me shaqarsa. Plat shoes tasaka a kafarta ta nufi falon,jin gidan shiru batayi tunanin Yana Nan ba Saida ta shigo sosai ta ganshi a kishingide da remote a hannunsa Yana kokarin canza tasha. Tashi yayi daga kishingidar ya zauna sosai Yana binta da wani mayen kallon, tunda suka hada ido sau daya Bata Kara yarda ta kalleshi ba. "Zo ga wayar ki Nan tunda Naga itama kinyi zuciya da ita kin bar min". Ya fada yana Mika Mata hannunsa alamar tazo ba musu ta nufo shi cikin takunta na nutsuwa, shi komai yarinyar Nan tayi burgeshi takeyi ga uwa uba Kuma ya fuskanci tana da tarbiyya da biyayya sabanin yanda yake kallonta, Bai zaci zata kwantar da hankalinta haka ba sai yaga ta tattara komai ta aje gefe abinda ya fuskanta kawai dai Bata daukar raini. Tana karasowa saita zauna kusa da kafafunsa a kasa taki zuwa gurin hannunsa da yake Miko Mata. Dan murmushi yayi Shima ya sauku Yana facing dinta da karamar ledar dake hannunsa, Mika mata yayi."Gata Nan ayi hakuri ki hada ta batirin ma yana da full charge da sim a ciki, duk numbers dinki important suna ciki. Wayar ta bude sabuwa ce Kar jujjuyata ta Fara tafi wadda ya Fara Bata tsada nesa ba kusa ba kallon tuhuma ta Farayi Masa tana girgiza Kai tare da Mika masa wayar tana Fadin. "A Ina kake samun irin wadan Nan wayoyin na mahaukatan kudi wlh ba ruwa na ka rike kayanka bana so ka maido min tawa ta asali kawai". ✨✨ ✨✨ ✨💎AUREN HUCE HAUSHI💎✨ Assalamu Alaikum warahamatullahi ta'ala wabarakatuhu. Dukkan yabo da godiya sun tabbata ga Allah s.w.a, salati da daukaka da Aminci su tabbata ga Annabin Rahama Muhammad s.a w.w. Page 25 📖🖋️ ________Dariya ya kama harda hawaye abinda bata taba gani ba. Sororo tayi tana kallonsa, ita bataga wani abin dariya ba a maganarta, hannu ya Mika ya karbi wayar kunnawa yayi ya Mika mata Yana kashe Mata ido tare da d'age gira. "Kina son kisan inda nake samun mahaukanta kudaden Nan ne?". Kai ta gyada Masa. "Good ki Bari sai ranar da Kika Zama ni na zama ke na mallaki kayana, a ranar nayi Miki Alkawarin sanin komai nawa na duniyar Nan, Idan Kuma yanzu you are ready za'a taimaki Dan Malam a lullubeshi da bargon ni'ima to? yanzu kuwa kisha labari har wanda Baki nema bama zan fad'a Miki, tunda ke inda nake samun kudi kawai Kika bukata baki son sanin waye ni?daga Ina nake?meya kawoni garinku? Gasu nan rab'ab'a da yawa, to ki rubuta ki aje har abada ni Mahmud bazan tab'a ciyar dake ko shayar dake ko wani Abu na jindadin rayuwa da haramun ba, duk abinda na Baki ki tabbata da gumin halalina na nema, kinga wannan wayar da kudina na saka na saya Miki,wato kina tsoron kada na Sato kayan mutane na kawo Miki ko?" Kai shiga gigizawa. "Ni ba cewa nayi kayi sata ba, gani nayi kana ta abubuwan da sai Mai wadata ne ze iya yinsu Kai Kuma Naga...." Sai kuma tayi shiru tana kallonsa. "Oya continue Mana,kinyi shiru wato Kinga bana aikin komai ko?". Shirun tayi Bata Kara cewa komai ba. "Tashi ni ki bani abinda zanci idan na biye Miki da wannan yarintar taki sai yunwa tayi min illah kisa a Fara gulmarki ace kina barina da yunwa, ganshi kin sani azumin da Babu lada". "Ba Kaine kayi zuciya ba ka tafi kabar abincin" Ta fada a shagwabe. "Ki tashi ki bani kada lissafin ya canza fa" Ya fada yana matsowa jikinta sosai, da sauri ta Mike ta nufi dining inda ta jera abinci. Table mat ta shimfida a Kan carpet din sannan ta dauko abincin ta aje. Plate biyu ta dauko dayan ya janye. "Ki Zuba Mana a plate daya ya Isa ai Kuma indai Ina gida plate din mu daya tunda Kika yimin horon yunwa yau daga Wasa Dan kawai kewar Hajiya ta ta kamani shine Kika horani duk ranar dana kaiki gabanta saina fada Mata tasan irin zaman da zatayi dake, ni Dan gata ne a gurinta bana laifi zakiga yanda take sona". "Ko?" Ta fada tana zuba abincin a plate, Dan tura Masa plate din tayi kusa dashi "Gashi Nan ni bana Jin yunwa". "Ashe zan Miki dura wlh, sai kinci kuji min yarinya da kinibibi Wai so kike da karfi sai kin koya min surutu ne? Kin iya kalato abin magana da wani bakinki chut". Ya fada yana shafo pink din lips dinta. Taci Amman ba wani na kirki ba da gaske abinci Bai dameta ba barta dai da 'yan ciye-ciye. Bayan sun gama ne ta kwshe kayan ta gyara gurin duk Yana kallonta komai tayi kyau yake mata gata ba wata babba ba sai dai akwai Sama da kasa masha Allah. Lokacin data gama ne ya yafito ta da hannu,a hankali ta nufo shi kamar me counting steps sai rausaya take, wani yawu ya hadiye, Dan risinawa tayi a gabansa duka hannuwanta ya kamo ya zaunar da it kusa dashi. "Zaki rakani unguwa?" Ya fada Yana zame Mata veil din da tayi rolling gashinta ne ya bayyana biki sidik dashi sai walqiya yake yasha gyara ga kamshin hair spray Yana tashi. "Eh zani Bari naje na shirya". ta fada Tana kokarin zare jikinta daga nasa. Duka hannuwansa yasa ya riko kugunta ya hade ta da jikinsa. "Ina zaki?wane irin Shiri zakiyi kinsan inda zamu ne kike sauri?". Lakwas tayi a jikinsa da karfi da yaji so yake ya Saba mata da Zama a jikinsa gashi baya ko Jin jauyin taba Mata jikin sai dai idan Bai soba. "Bazaki tambayi inda zamu ba, kina Neman sake canza Kaya". "Nasan gida zamuje Mana". "Ai kece gidan, kinaji da so nake muje gidan da gaske mu roki alfarmar a bamu aron me aiki daya Wadda zata zauna min dake kafin na dawo". "Kafin ka dawo? Ina zakuje?". "Au Ashe ban fada Miki ba, aikin NGOS din Nan ne ya taso suka gayyace mu zuwa meeting da zasuyi a UK Kinga ai bazan zauna ba da dollars ko stalling founds suke biyan mu, idan Allah yasa na samu da Dan auki Kinga na Kara jarina tunda Naga Nima Ina sha'awar siyar da materials har munyi magana da Abba yace ze bani rumfa daya a Muda lawal market na gwada ko ina da nasibi a cikin sana'ar, sannan Habib ma munyi magana zamu Fara siyar da spare parts na motoci a nan Muda lawal market din dai". "Allah ya bada sa'a, Kuma idan ka tafi sai yaushe zaka dawo? Ko kaima shike Nan abinda yake faruwa Dani ze faru a kanka kaima, kada ka tafi ka barni Dan Allah tunda nasan ba Sona kake ba baka ni akayi sadaka, Dan Allah ka taimaka ka kaini Jordan tunda Ina kudin flight kawai ka taimaka ka fitar Dani daga kasar da sunan Kai zaka tafi dani, bana son Ammah ta qara shiga cikin damuwa a kaina wlh Batasan tashin hankali ba Sai Dana isa aure Kullum idan kaga Ammah a cikin tashin hankali to a kan lamarina ne ni Kuma yanzu bana fatan na qara ganinta cikin bacin rai ta dalilina, kaje ka fada musu zaka tafi Dani ko Kano ne ka Kaini na zauna gidan su bestie kafin na samu visa, nagaji da Kasar nan wlh Ina da gata Amma sai walagigi rayuwa ta takeyi anan Dan Allah kayi min wannan alfarmar Koda ita kadai zakayi min ta karshe a zamana da Kai". Ta kifa kanta a jikin kafad'arsa ta saki wani kuka Mai tsuma zuciya. Bai hanata ba ya dai Kara matseta a jikinsa Yana shafa bayanta yasan abin Yana cin zuciyarta ne bata rasa komai ba amma an dabaibaye Mata Jin dadin rayuwa kamar yanda Baba malam ya fada masa. Sai da tayi Mai isarta ya dago kanta daga jikin kafadar tasa. "Kiyi hakuri kowa da irin tasa jarabawar ke taki a haka tazo, Kuma waya fad'a Miki zan tafi na barki bazan dawo ba? Waye kuma yace Miki bana sonki? Kinsan tun tsawon lokacin da nake dakon soyayyarki kuwa? Tun Baki san meye son bama yarinya share hawayen ki Mahmud naki ne har abada, dole kije Jordan ke me gida sukutum a can.Amma yanzu kiyi hakuri nema zani idan Kuma na zauna bakya son tafiyar saina fasa Sameer yayi komai kawai nace madam ta Hana". "Kaje kawai idan baka dawo ba nasan abinda zanyi". "Keh! kina da hankali kuwa me zakiyi wlh zan turaki gurin Hajiya Inna duk da ban shirya zuwa yanzu ba kawai ki Kira min ruwa, zaman Allah nakeyi zamanki nakeyi badan ke ba Dana Dade da barin garin Nan". " Ni Kuma?" "Off course" Ya fada da karfin gwiwa. "As how?" Share ta yayi kamar bai jita ba. "Tashi ki rakani kada dare yayi, dauko Mana key din motarki na dana kada na tafi ban Sanya albarka ba, ki canza shiga kada a kalle min kayana" fada Yana mikar da ita daga jikinsa. Duk kin haye min cinya kinsa sai ciwo take min". Ya fada Yana Mata wani smile. Bata kula shi ba tayi gaba abinta duk zuciyarta ba Dadi sannan tana jujjuya maganganunsa a zuciyarta, kinsan tun lokacin da nake sonki? Danke nake zaune a garin Nan gasu Nan dai da yawa. Saida ta sakarwa Kanta ruwa sannan ta shirya agurguje ta saka wata Riga da siket na atamfa super dinkin ya zauna das a jikinta ta saka mayafin da yayi matching da atamfar ba tayi amfani da turaren kaya ba body mist kawai tayi amfani dasu a jikinta kusan kala uku, sai ya bada wani sansanyan kanshi Mai dadi. Tana gyara gyalen ya shigo dakin tsayawa tayi tana kallonsa shida yace unguwa zata raka shi sai gashi da Riga armless da wandon ta farare tas na kamfanin Adidas sai taga kwata kwata ya canza Mata ya koma irin 'ya'yan hutu din Nan na gaske wadanda Jin Dadi ya gama ratsa su yayi wani irin fresh da shi. Matsowa yayi kusa da ita Yana Dan watsa hannu irin dai na isassun yaran. Mayafin ya kama ya ida rufa Mata a kanta. "Kallon fa na menene? Kona canza Miki ne?". Kai ta girgiza Masa. "Baba son body language fa ki bude Baki kiyi min magana". Yana janyo ta jikinsa. "A'a kawai dai da naji kace unguwa zan rakaka kuma na ganka da......" Sai tayi shiru. "Karasa Mana sai Kika ganni da shigar nigas ko?" Shirun dai tayi. "Idan Ina tare da iyalin dole na sake, kema da nace ki canza ai na Shan iska nake nufi ba Wai irin wannan ba, zo muje ki canza yawon Shan iska zamu ki min hira ki bani labarin ki tunda ke bakya bukatar nawa ki bani happiness a wannan Daren yanda duk inda nake na rinqa Tino da abubuwan su zamar min kamar kina kusa Dani". "Ni dai Dan Allah ka barni haka muje kawai" "Dauko key din to muje dare nayi Kuma Ina son ganin Baba malam da Abban mu, ko ba namu bane?" Ya fada Yana kallon ta, an samu cigaba, tunda ko banza tunda ya mamnatse ta take iya kallon idanunsa ba kamar da ba da Bata yarda ta kalleshi. "Namu ne". Ta fada a hankali, badan Yana very closer to her ba da ba lallai yaji me take fada ba. "Oya let's go". Ya fada Yana nufar kofa, saida ya kashe electronics na gidan sannan suka fito Yana time da karamar luggage a hannunsa,Kati ya curo daga cikin wallet dinsa ya saka a kofar ya rufe, daga nesa Mai gadi ya hangesu sun nufi parking lot din gidan inda motar daya take ajiye, a ransa yake fadar "duk inda wannan Dan ya fito Dan mafita ne ba irin yaran Nan bane lalatattu kamar yanda aketa surutun abun masu kushe da ganin rashin kyautatawar su Alhaji nayi masu gani kyautatawar nayi". Yana can Yana tunani Bai ankara ba yaji Karan Horn alamun har sun karaso Yana can Yana nashi zarafin. Da gudu ya tashi Yana fadin Ayi hakuri nayi zurfi gurin tunani ne, a dawo lfy Allah ya tsare". Horn ya yi Masa suka fice daga gidan. Suna barin gidan sun hau babban titi sosai motar su mama ta doso kofar gidan. Dan saida suka hada turaren wutar ya kammala aka zabga Masa turarika masu mahaukatan kanshi da mazubai Wanda dole yayi attracting mutum. Daga Dan besa direban ya tsaya Mama da Asabe suka fito Asabe na rike da ledar Mai tambarin gurin Saida turarukan wutar dasu humra suka nufi gate din gidan, Asabe CE tayi knocking ta 'yar karamar kofar jikin gate din ya leko ya gane Mama tunda ya jima a unguwar sai dai ita ba lallai yasan shi ba. Da sauri ya bude kofar Yana fadin. "Hajiya kune haka barka da zuwa ina wuninku". Ta rusuna ya gaishe su. 'yar dariya Mamar tayi tare da amsawa kafin tace masa. "Munzo Kara duba Zahra ne tunda tazo ban samu mun shigo ba sai yau" Cikin nuna girmamawa malam Sani yace. "wallahi kuma anyi sabani yanzu ba dadewa suka fita da Mai gidan da kun lura ma inaga kunyi kiliya dasu a lokacin da zaku shigo su Kuma sun fita". Turus sukayi wannan ta kalli wannan. "Ina suka fita daga kawo yarinya ko sati Bata rufa ba?" Ta fada da alamun bacin rain a maganar ta ta. "Wlh nima ban Sani ba tunda ba hurumina bane sanin hakan ba, sai dai ko Zaki Kira ta a waya idan basuyi nisa ba sai su dawo". Mama Bata taba danasanin rashin karbar number zahrar ba irin yau. "Ba komai ga sako Nan ka aje mata idan Allah ya kaimu gobe Asabe zata dawo tayi Mata bayaninsa" Ta fada tana kallon Asaben, Wadda ledar ke Hannunta, da sauri ta mikawa Mai gadin tana fadar "in Sha Allah zan shigo Amma a fada Mata". "In Sha Allah za'ayi fada kin gaida gida". Ya juya da ledar a hannunsa, want abu Asabe ta radawa Mama a kunne tayi saurin tsayawa tana duban kofar da Mai gadin ke kokarin turowa. "Malam Bismillah". Ta fada Tana komawa tare da dauko Abu a cikin Jakarta. Dawowa yayi Yana Dan sadda kai, kudin da Bata San ko nawa bane Mika masa. "Ga wannan ba yawa Dan Allah a tabbata sakon ya shiga Hannunta komai dare" "In Sha Allah Hajiya da shi zata shiga ciki, Allah ya Kara sutura na gode madallah". Ya fada Yana qara gyara rikon ledar da kyau. "Hajiya ta haka akeyi Nan gaba ko wani aikin kike bukata da gudu zeyi Miki kinsan su bugun Abuja ba bayanin da basa ganewa in dai kina ungo to zance ya Kare Abu sai dai in Baki nema ba, ai Nima goben da sako zan taho Masa Naga alamar kamar zeyi son abin duniya jifa yanda yayi caraf ya karbe kudin daman kamar jira yake. Dariya sukayi gaba daya harda tab'awa, suka nufi motar data kawo su. ****** Tafiya suke yi Yana rike da Hannunta da nasa dayan, dayan Kuma Yana tuki cikin kwarewa lokaci lokaci Yana Dan matse hannun, ganin sun dauki hanyar barin garin yasa Zahra ta Dan dube shi. "Wai Ina zamu ne?". "Siyar dake zanyi, kinji yanda nake samun makudan kudina cikin sauki, duk garin da naje haka nakeyi na duba kyakykyawar mace na aura idan an sake Dani sai nabi dare na gudu nabar garin daman ba Wanda yasan daga inda na fito, bare ke yanda Allah ya surantaki da sura ai ke sai nafi samun alheri a jikinki". Ya fada Yana wani daure fuska. Zuruzuru Zahra tayi ganin fuskarsa ba annuri ko misqala zarratin Nan da Nan jikinta ya dauki rawa, duk sanyin ACn dake motar Saida gumi ya rufeta, kallonsa ta Karayi still dai fuskar kamar bai taba fara'a ba a duniya. Jikinta tsumar ya karayi kamar ana kada Mata gangi, cikin sarkewar murya ta Fara magana bakinta Yana rawa. Me nayi maka zaka cutar Dani?". Rage gudun motar yayi cikin duhu, a hankali ya tssyar da motar, Zahra rufe idonta tayi take hawaye suka wanke mata kumatu. ✨✨ ✨ AUREN HUCE HAUSHI Maman Fateemah Page 26. ________Sai da ya gangare sosai sannan ya kashe motar, chak ya daukota kamar 'yar Baby ya rungumeta, dai dai kunnenta ya kai bakinsa ya hura Mata iska duka tsikar jikinta ta tashi duk da tana cikin halin rudu bai Hana sakon zuwa ba. "Ki rufa min asiri ada ace satoki nayi Nan da Nan kin rikice nayi Miki Kama da masu irin wannan d'abi'ar? Wlh zolsyarki nakeyi haka Zaki shide min ki Kira min ruwa daga fita unguwa mu bige da kwanan Asibiti cool down idan na sayar ai Nina kashe kaina". Ba zato taji ya saka harshensa Yana lashe hawayen Yana Wasa da harshensa a saman idanunta, qanqameshi tayi, "Dan Allah ka bari". "Na bar me?" "Hakan ba Dadi". "To da cewa nayi kiji Dadi? Ni nasaka kukan Kinga ai shanye hawayen ya kamani kada muje inda zamu a juya min baya". Ya fada yana shinshinar gefen wuyanta. " Kiyi hakuri bazan Kara ba tunda wannan idon naki Mai arahar kuka ne Ni zanga yanda za'ayi idan abin kukan ya samu". "Cewa fa kayi ka Saba halinka ne ka Saba yin hakan Kuma fa fuskar ka ba Rahama a ciki kamar Mai tsaron gidan wuta". "Kai innalillahi! Mai tsaron wuta ni din?" ya fada yana fiddo idanu waje "A'a ba Kai nace ba kamar nace". "Ba cinya ba kafar baya" " Nifa nayi ne Dan Naga idonki, idan kina cikin halin tsorata yana sakani nishadi". Wayar sa ce ta Fara vibration a jikinsa, Dan zameta yayi daga jikinsa ya dauko wayar ya duba tsaki ya d'an Yi. "Dan matsala kawai". Ya fad'a yana saka wayar a handsfree. "Ya akayi Hayatu". Dariya ce ta kwacewa Sameer Wadda Bai shirya Mata ba. "Wlh zan kashe, wato abin dariyarka na Zama ko?". "Sorry sir wlh ji nayi gaba daya tazo min, Kuma ko sallamar da nayi baka amsa min ba". "Ka Fadi abinda zaka Fadi Kona kashe da gaske Kuma sallama na amsa Kaine dai bakaji ba, duk safiyar Allah baka tashi kirana ba sai yanzu da tsohon dare salon ka Hana mutum rawar gaban hantsi, na fada maka idan Ina bukatar Abu ni zan nemeka Amma tsabar saka ido sai ka kirani ni, to fad'i meya faru? Ina jinka". Ya fada Yana maido ta jikinsa. "Game da maganar tafiyar Nan ce anya zanje kuwa wlh jiya danaje sokoto daukar wadannan hardcopy din na shiga gurin Hajiya Inna muna cikin magana saiga uncle Mustapha ya shigo a sukwane bansan wane minafikin bane ya fada Masa nazo garin ba tunda bana zuwa lokacin da suke gida, ya tasani gaba da sababin nasan inda kake ina kallon su suna walaqiqin nemanka Amma nayi mirsisi naki fad'a musu komai, Ni Ina ta faman lallaba mutuniyar taka amma Saida Uncle mustapha ya Bata lamarin Dan wlh kuka take da hawayen ta bibiyu tana fadin Dan Allah na fada Mata idan mutuwa kayi saita hakurw tasan ita kadai zata nesanta ka da ita, wlh yanda ta bani tausayi da bude aiki kawai zanyi sai Kuma na tuna da warning dinka kawai na fasa, Kuma wlh yanda uncle yayi ba abinda ze Hana shi bibiyata ta karkashin kasa ban sani ba a gida da waje amma ya kake ganin za'ayi? Numfashi ya sauke me karfi yana Kare matse zahrar a jikinsa har Saida tayi 'yar karar Jin zafi. "Karar me nakeji a kusa da Kai ne?". "Ina ruwanka tsabar saka ido, to madam ce a kusa Kona baka ita kaji for confirmation, a'a Barta a gaisheta". Tana jinka a speaker wayar take, ka Bari kawai Zancen baze yuwu ta waya ba idan Allah yasa na shigo sai mu tattaunawa Kuma ka tabbata komai ya kammala kafin na shigo goben in Sha Allah" "Noted, in Sha Allah a gashe min da ita sosai a fada mata Batool tayi ta kiranta dazu ba'a dauka ba". "Ina ga a gida ta baro wayar ka ganta Nan sai rigima take zabga min irin tasu ta shagwababbun 'ya'yan larabawan" ya fada yana dan matse dantsen Hannunta kadan. "Wash Allah na da zafi fa". Ta fada tana Masa wani kallo Mai ma'anoni kala kala. "Allah ya bamu Alkhairi" Sameer ya fada Yana kashe wayar Bai jira yaji abinda Mahmud din ze fada ba. "Kinga kinja ya katse Kiran bamu gama bayani ba irin wannan Abu haka ai sai ayi zaton muna hanyar shuga wata nahiyar ne". Sunne Kai tayi a jikin kirjinsa, "Dan Allah ka Bari ni me nayi,". "Ba komai". "Bayani zakiyi da yaren garinku yarinya". Gurin zamanta ya maida ta sannan ta tada motar suka koma kan titi, tunda zahra ta koma gurin zamanta take Masa kallon tukuma da neman Karin bayani. Amma saiya fuske abunsa kamar be gane ba, Yana ta faman tukinsa ko a jikinsa. Zaranda hotel taga sun shigo, kallon mamaki tayi Masa a kasan zuciyarta tana tunanin me kuma za'ayi a Nan shida yace unguwa zata raka shi to Wai mema ya hada shi da hotel ne? Gurin da aka tanada don parking ya nufa ya kashe motar. Fitowa yayi ya zagayo kofar da tare zaune ya bude ya Mika Mata hannunsa ta Kama ta fito. Kulke motar yayi ya jata suka nufi ciki, a Hanya suka hadu da wani security da gani akwai sabo sosai a tsakaninsu. "Ranka ya Dade an shigo lfy? Ya fad'a Yana kallon Zahra a kaikaice. "Lafiya kalau Ibrahim ya aikin?" "Lafiya kalau yallabai". Ya fada Yana niyyar wucewa yana Kara kallon Hannunsu dake sarke Dana juna. " Ibrahim gafa madam Dina Yau na kawota taga mafakata". Ya fada Yana Dan murmushi. Dawowa yayi Yana fadin. "Masha Allah yallabai Allah ya bada zaman lfy, ai Dani aka daura Auren babban masallacin juma'a, madam sannu da zuwa gurin namu". Ta amsa ta gaishe shi ya amsa yana Mata Allah Sanya Alkhairi sannan sukayi gaba, dakin da yake kusan mallakinsa ya bude musu suka shiga lumshe ido Zahra tayi Dan wani special kamshi da sanyi A/c ne ya bugeta, yanayin ba Karamin Dadi yayi Mata ba, direct kan sofa ya nufa da ita tare suka zauna har lokacin Bai sakar Mata hannu ba. Falon tabi da kallo ba karya komai yaji Dan an kawata shi sosai. "Wai me zakayi a nan?" Ta fada tana masa kallon ido cikin ido. "Me kikeci na baka na Zuba? ai dai muna tare dake ko! zakiga abinda zanyi yanzu ki zauna ki dan tayani aiki kafin naje unguwar ku gurin iyayena sallama". "Dan Allah kaje Dani " "Kai ! Naje dake Ina? Lallai kina so na amsa tambayoyi kenan kwanan ki nawa rabonki da gidan? Kawai na kawoki Nan ne kisan dakin yana cikin abubuwan da suka zamar min abin tunawa a zamana na garin Nan kinsan saboda ke na kama shi ya Zama permanent dakina tsawon shekara kusan biyu da nayi a garin nan?". Galala take kallonsa. "Saboda Ni kamar Yaya?". Wani kallo yayi Mata Yana Dan taune gefen lips dinsa na kasa. "Naki Wasa ne yarinya,Wai kin zata daga cewa an bani Mata saina karba kawai? Niga sarkin tausayi ko to Daman Nima Ina son kayana kawai dai kinfi karfina ne na mikawa Allah kukana Ina zaune Kuma ya juya lamarin gareni tunda shiya hadani dake a inda ban zata ba ya cusa min soyayarki lokaci daya nasan baze Bari na shiga gararin rayuwa ba, duk rintsi ze kawo min mafita sai gashi ya kawo min lokacin da har nayi given up Ina kokarin barin garin idan na shaida dauri Aurenku, amma fa da Allah kadai yasan meya faru yanzu to Sai ya taqaita cikin shikimarsa". Agogon hannunsa ya duba, Zahra tana kokarin magana ya katseta. "Adana tambayar saina dawo Kinga idan na biye Miki ba inda zan fita, a 'yan kwanakin nan kin mayar Dani wani parrot sai magana nakeyi ba comma ba full stop, wlh kin canzani kwata-kwata da Hajiya Inna zata ganni Ina zuba haka hum..". Ya fada Yana daukar luggage din daya shigo da ita da dayan hannun dayan Kuma ya mikar da ita tsaye. "Zo muje ki tayani shiryawa". Nokewa tayi tana Dan ware idanunta. Shiryawa kuma? Kaje kawai Ni ina nan". Gaba yayi yaga alama da gasken ze iya shashancewa a gurinta. Komawa tayi ta zauna tana jujjuya lamarin bawan Allahn nan sai wasu maganganu yake fada Mata ba tare da fashin baqinsu ba. Kamshinsa shiya fada Mata wanzuwarsa a falon, a hankali ta dago Kai ta kalleshi "Masha Allah" ta fada a hankali Dan ba lallai yaji ba. Gurin da take zaune ya Dan tsuguna a gabanta ya Dora Mata laptop din dake hannunsa da wasu takardu da list na sunan mutane kusan dari da ashirin da biyar daga local government hudu Alkakeri, Jama'are, Zaki da Dass, karkashin makarantun Allo zasuyi step down training a Nan Azaren schedule ne na aikin da payment dinsu. Ta dago zatayi magana ya Dora Mata yatsa a biki "kiyi kawai idan na dawo kin tambayeni duk abinda kike bukatar sani bana son nabar garin Nan aikin Nan Bai kammala ba". Ya Mike fuskarsa ya kawo dad da tata ya Bata light kiss a gefen kumatunta, saina dawo take care". Ya nufi kofar da sauri da key din motar a hannunsa. Harya rufe kofar Bata dauke idonta daga gurin ba, ita fa mutumin Nan ya Fara Bata tsoro mutane suna daukarsa wani Abu daban ita Kuma tana ganinsa wani Abu daban. Ta Dan jima Tana sakawa da kwancewa daga karshe ta watsar da komai ta dauki laptop din ta shige cikinki bedroom din ta Haye lafiyayyan gadon ta bude ta shiga aikin inda Allah ya taimaketa yaci karfin aikin karasa Masa zatayi. ******* Lokacin da Mahmud ya fito Ibrahim da wani sulaiman ya Kira ya Basu aikin kula da dakin da Zahra ke ciki duk da yasan suna da matakan tsaro sosai Amma hankalinsa Bai kwanta ba sai da ya Kara Mata da nasa, gurin motar ya nufa bayan ya zauna ne ya Ciro wayarsa ya bude ta haka Nan ya shiga CCTV da akayi connecting da wayarsa. Hotunan ne suka fito rababa na dakinta yayi zooming qura Mata Ido yayi lokacin data fito daga wanka tana daure da Karamin towel fararen cinyoyinta sunyi wani sambal dasu ta Kai ta kawo Yana kallonta harta gama, tunda ya Fara kallon yake sakin wani Nishi kadan kadan Dan da gaske ta yamutsa Masa tunani ji yake kamar ya zubar da Alkawarin daya daukarwa kansa a kanta, komawa yayi baya na kofar gate ya dauki hankalinsa ganin wata mota mata sun fito sun dauko wani Abu a Leda sun nufi gate din gidan full screen yayi da gurin da suke ya waye da mama amma Asaben çe bai ganeta ba yana kallon duk abinda sukayi har Zuwa lokacin da Asabe tayiwa Mama rad'a a kunne ta Kira Mai gadin ta bashi kudi suka juya da yanda suke kwasar dariya har da tabawa kamar yara sai abin ya bashi mamaki, meya kawo su gidan su kadai ga Kuma motar da gani ta commercial ce, girgaiza Kai kawai yana tunanin abinyi. Da gurin malam ya fara zuwa ya Dan jima tare dashi kafin ya aje Masa Alkhairi yayi Masa sallama, Yana Kara yi Masa addu'ar samun nasara a tafiyar da godiyar Alkhairnin daya bashi, Habib ne ya Dan kalli Mahmud din bayan sun fito Yana tambayarsa.. "Da gaske baka fad'awa Baba malam ba inda zakun kada fa yaji daga baya yayi fada yace ka tsallake kasa baka fada Masa ba. Kafadarsa ya dafa. "Kada ka damu da kaina Zan fada Masa in sha Alllah". Tare sukaje gidansu Zahra inda suka Dace suna kokarin yin knocking sai magaji ya fito, daga gani wani gurin zaya yanda yayi Shar dashi. Gaggaisawa sukayi kafin Magajin yayi musu jagora zuwan gurin Abban nasu. Anan falon ganawa da bak'insa suka sameshi, sun gaisa Sosai a Nan Mahmud ya fada masa tafiyar da zeyi, Abban yasa Albarka soshi. . ✨✨ ✨✨ AUREN HUCE HAUSHI. MAMAN FATEEMAH Page 27 _____Dan Jim Mahmud yayi kafin ya Dan muskuta kadan ya Kara sadda kansa kasa. "Abba Dan Allah ko za'a taimaka a bamu Aron daya daga cikin masu aikin Nan Mata su tayata Zama kafin Allah ya dawo damu". Ya fada a ladabce Dan gyaran murya Abban yayi Yana fadin "Hakan babu laifi kayi tunani Mai kyau baza'a bar yarinya ita kadai ba gara da babba, ba komai kome kenan da safe za'a turo wadda zata zauna da ita, Allah yayi Albarka ya bada sa'a" Sun jima suna Hira da Abban har suke fada Masa harkar kayan spares na kayan motocin da zasu ringa saidawa, Albarka ya sanye musu sannan sukayi Masa sallama, har sun Kai kofa Abban yace Bari ya fadawa Ammah ku shiga ku gaisa, a waya ya kirata ya fada Mata sannan yace su karasa ciki. A kofar gate na shiga ciki suka samu Musaddiq Yana jiran su, cikin ladabi ya gaishe su Yana tambayar Mahmud Aunty Zahra, hannunsa Mahmud din ya Kama Yana bashi amsa har suka shiga part din Ammar. Sallama sukayi tana zaune a parlourn, sallamar ta amsa tana fadin. "Su Habib ne sannunku Bismillah". Ta fada tana nuna musu gurin Zama. Basu zauna a kujerar ba sai suka zauna a Kan carpet. "Ina yini?" Suka fada a tare, "lafiya kalau ya wajen malam?" "Lafiya kalau yace a gaisheku". "Masha Allah muna amsawa, Allah yayi Albarka, yayi muku jagoranci cikin dukkan lamuranku, ayi ta hakurin Zama da yara". Ta fada a kunyace Dan har ga Allah tana Jin nauyin yaron da kaunarsa saboda karamcinsa da halin fattako daya nuna lokacin da aka bashi Auren zahra da Rana tsaka ya Kuma sa hannu biyu ya karba. "Amin na gode ba komai, zahrar tace ma a gaisheku, kuma nazo ne nayi muku sallama zanyi tafiya ne amma in Sha Allah bazan jima ba, na fadawa Abba a samu wadda zasu zauna tare kafin Allah yasa na dawo". "Masha Allah. Allah yayi taimako hakan baze gagara ba ko can gida Mubi Sai a samu wadda zatazo su zauna tunda akwai yaran sosai ba sai an dauko bare ba tunda yau din ta Zama wata iri Amma kafin tazo sai su Fara Zama da zulai tunda Bata da matsala" "Godiya muke Allah ya kara sutura" Habib ya fada, suna mikewa har lokacin Autan Ammah Yana jikin Mahmud a zaune. Addu'a Ammah take musu har suka fito Nan da nan wani rauni ya shigi Mahmud haka tasa Umman take Masa a duk lokacin da ze shiga wurinta bakinta baya gajiyawa da Yi Masa addu'a, duk kewarta sai ta rufe shi, "kaimu gurin Mama mu gaisa". Mahmud ya cewa autan Ammah. Part din Mamar suka nufa, Musaddiq ne yayi knocking har sau biyu ba'a bude ba Kuma suna jiyo maganganu da sound din tv. Habib ne yace "mu tafi Dan Allah yaushe zamu tsaya kamar wasu 'yan maula". Har sun sauka daga steps din balcony din sannan aka bude kofar, Asabe ce ganin Autan Ammah da mutane yasa ta fito tana fadin ku shigo Dan Allah wlh bamuji ba sai daga baya Salma ke fadin Kamar taji bugun kofa". Habib ne yayi farat yayi magana "ai ba komai a gaishe da Hajiyar Daman mujin Zahra ne ya shigo ya gaishe ta". Sukayi gaba suka barta a tsaye. Ciki ta koma jiki ba kwari. Mama ce ta kalleta. "Wai su waye Naga kin fita Kuna magana dasu ne Kuma Basu shigo ba?" Zama tayi kusa da mamar, "sirikin ku ne inda mukaje basa Nan yazo gaishe ki da alama Kuma sauri suke tunda sun jima a tsaye ba'a bude ba". "Wai kina nufin Mahmud mijin Zahra?" "Shifa sunce a gaishe ki, da alama sauri suke Dan har sun fice. Baki Salma ta tab'e tana fadin. "saura kiris dai uban kowa ma ya rasa, ba dai kunce kun Kai turaren wutar ba, yanda aka wayi gari aka ganshi da hakoransa talatin da shida haka za'a wayi gari yayi layar zana inga ta qafafar da ake anyi aure, auren ma Dan jeka nayi ka da ba wani armashi yayi ba, Shima Abba Dan ya ganshi handsome ne ya bashi ai ko banza ance mijin agolar gidansa ne". Dakuwa Mama tayo Mata "Abban naki kike fadawa haka? Nima da farko nayi tunanin ko wani lashi yaga yaron Yana dashi sai da na saka akayi min bincike aka tabbatar min da gidan da kayan da yake sakawa duk Wanda yakewa aiki ne suka kawo Masa Dan wasu ma ance min wannan yaron shugaban aikin nasu ne ya kawo Masa kwancensu Dan ya rinka fita kunya tunda matar tasa 'yar boko ce, shi Kuma almajiran soro ance min ma iyakarsa secondary ya Dan iya rubutu da karatu ne yasa suka dauke shi aikin nasu, har kike wani zaqewa kina sonsa ai da naji haka saina fad'i ba nauyi yo Dan kyau me ake da kyau bako sisi Allah Banda nayi Alkawarin saina Maida Zahra karamar bazawara ba, da barinsa zanyi a garin to idan nayi wannan saken kakanninta zasu iya bashi mahaukatan kudi ya nemi sana'ar da ze rike musu jika gara dai yayi gaba tazo ta zauna na Dora daga inda na tsaya". Dariya Salma da Asabe suka kwasa Asaben ce ke fadar "Aikinki Yana kyau uwar dakina ba Wanda ze taba hasaso hakan daga bangaren ki kin kasa kin tsare duk wata kafa da wani ze fahimci da saka hannunki a lamarin yarinyar nan". Dariya mamar tayi itama "Au da sokike na ringa nuna adawata a fill ai Ni duk ranar da tazo gidan Nan da bayanin mijin ya gudu sai nafi kowa kuka da tsine masa". "Sai Maman mu". Salma ta fada tana kyalkyalewa da dariyar mugunta. ********* A harabar gidan suka samu Abba Yana yiwa malam Bala direba magana, gurin suka nufa Abban na ganinsu ya nufo inda suke. "Har kun fito" "Eh Abba zamu koma" Suka fada tare, takarda Abban ya mikowa Mahmud. Hannu yasa ya karba. "Gashi Nan ka Kara guzuri Allah ya kaiku lfy ya bada sa'a". Godiya sukayi Masa sosai har Saida yayi fada. Tare suka fita da Auta har gurin mota ledoji biyu Mahmud ya dauko daga seat din baya ya mikawa Musaddiq. "Gashi naka daya na Faruq daya tukwaicin ku ne na kawo abinci". Da murna Auta ya nufi gida Yana fadin "mun gode Uncle". Cheque din kudi ne masu nauyi Abban ya bawa Mahmud saida abun ya Basu matukar mamaki. Habib ya mikawa cheque din Yana fadin. "Ka rike a gurinka kawai a sawo kayan shagon Nan dasu a Fara kasuwar tunda Allah ya kawo kawai". "A'a baza'a yi haka ba ka tafi dasu kayi guzurin Kamar yanda yace idan Allah yasa kun dawo sai asan yanda za'ayin". "Kayi yanda nace ba wata damuwa acan komai Yi Mana za'ayi to me zanyi dasu? ga Kuma abun bukata a gida ba gara ayi ba watakila kafin mu dawo ka koma sari na biyu". Ya fada Yana murmushi. Majalissar su sukaje Mahmud yayi musu sallama har salisu Yana zolayarsa akan barin Zahra da zeyi Yana tsakiyar angwancewa. Bai Dade ba ya tafi duk hanlalinsa Yana kanta yasan har ta gaji da jiransa watakila ma tayi barci. Saida ya biya ya saya musu kaza da apple ya dauki hanya. Lokacin Sha daya da minti ashirin da bakwai. A hankali ya bude dakin abin mamaki Zahrar ya gani gurin fridge da glass cup a Hannunta tana Shan wani abu, Sam bataji bude kofar ba saboda tv a kunne take sannan ta bawa kofar baya, Jin kamshin turarensa yasa tayi saurin juyowa lokacin yazo daf da bayanta, juyowar da tayi sai a cikin kirjinsa. Ledar ya saki qasa yayi Mata kyakykyawan masauki ya saka hannunsa ya talkafo bayan ta, yasa Bakinsa a dai-dai kunnanta. "Na dauka kin wuce Kano a barcinki Ashe dai jaruma na aura wadda take iya jiran mijinta komai dare". Ya karasa fada Yana Dan hura Mata iskar Bakinsa a kunnen. "Dan Allah ka Bari". Ta fada tana niyyar janye jikinta shi Kuma ya Hana hakan. Dan kwabe fuska tayi, "ka sakeni toilet zani". "Ba wani toilet idan Kuma da gaske ne muje na rakaki". Kai ta gigiza, shafa gefen ribs dinta yayi yaji yanda rigar ta matseta komai yayi tsan-tsan. Dan sakinta yayi Yana Kare mata kallo daga sama har kasa, Dan sunan dinkin a tsokano fitina kawai, shi a dazu ai be karewa dinkin kallo ba sai yanzu a kausashe ya jefa Mata tambayar. "Waye telan da yake Miki dinki". Hannu yasa ba zato ya shafo gaban rigar da sauri ta saka duka hannuwanta ta tsuguna sai Kuma kasan ya baje. "Ya Salam" ya fada a hankali. "Kinyi shiru Ina tambayarki". "Makociyar Aunty Hasana ce take Mana dinki". Ajiyar zuciya yayi yayi zaton namiji ne yaji ance sune ke gwada Mata idan hakan ta kasance ai an gama dashi wani ya taba Masa wannan jikin. Tsugunawa yayi ya kamota ya dago jikinsa ya maidata "ki barni naji duminki gobe ya wannan bana kusa dake Ina can na rungumi pillow, so muje muyi hirar yaushe gamo, ko Kuma ban sani ba murna kike kina Jin dadin Zan tafi na Baki space ki sake ko?" Ya fada Yana Wasa da Dan Karamin zoben dake 'yar karamar yatsarta. "Oya talk kinyi shiru koba haka bane daman ba kince min me naci Kamar maye na tsotseki waya sani ko maye ne ni ko Baki fada ba? Kawai Dan na koyawa bakinki ladabin magana da miji akan wannan yaron shine na samu lambar maita daga gurinki". Sexy eyes dinta ta zaro Masa, abinda yake burgeshi yake matukar so kenan yaga ta tsorata. "Ni nace maka maye? Yaushe akayi hakan Wana fadawa?" "Abar maganar kawai sai ranar Dana cinyeki danya Zaki gane Ni maye ne". "Wlh Ni ban fada ba, Toni Wana na gani da Zan Fadi haka har a Gaya maka, a kwanakin Nan ko waya ban rike ba fa". "Naji shike Nan zo muje Naga aikin Allah yasa dai yayi kada aiki ya Koma baya" Ledar tsarabarsa ya dauka ya jata suka nufi ciki. Gefen gadon ya zauna Yana janyo laptop din gefensa Zahrar na tsaye a dayan gefen. "Hayo ta Nan ki bude ki nuna min aikin in gani". Ba musu tayi yanda yace Kan cinyarta ya Dora laptop din ya Dan kwanto jikinta yana ganin aikin har ta Gama nuna Masa, tab'a hannu yayi Yana fadin "inye kice idan Allah ya hure mun na samu sakatariya ta a gida basai na nema a waje ba, yanzu jeki saman fridge akwai plate biyu ki dauko kizo ki Zuba wannan" ya nuna Mata ledar daya shigo da ita. Laptop din ta aje kusa dashi ta janyo gyalen da ta yafo zata yafa ya karbe Yana Mata wani kallo. "Me zakiyi da shi ko akwai Wanda ba muharraminki ba a Nan da Zaki Kama rufe jiki, ok da bana Nan kin aje har Dan kwalin kina watayawa yanzu Kuma na dawo Zaki wani saka gyale tunda idan na ganki kin dauki zunubi ko?" Shiru tayi Masa tasan idan ta magantu sai ta Kara laifi, juyawa tayi ta nufi kofa ya bita da idon Yana kistima abubuwa da yawa a zuciyarsa. Plates din ta dauko ta kawo ta koma ta dauko ruwa roba daya da fresh milk tunda taga Kamar yafi son Shanta akan lemo. "Dauki ki zuba" Nan ma ba musu ta bude kedar Naman wani kanshi ne ya doki hancinta har lokacin Kuma da zafinta, daya ledar ta bude apple din ta Zuba a kai, gyara zama yayi Yana nuna Mata gefen shi, Kaita girgaiza. " Na koshi bana Jin yunwa". "Naji ai ba abinci bane kizo kici ko nayi Miki dura da gaske nakeyi fa". Narai narai tayi da ido, Allah bana cin Abu Mai yaji ko maiko da yawa da dare ulcer yake tada min". Ture plate din yayi gefe ya janyota ya zaunar da ita a cinyarsa. "Me Kika ce? Ulcer as how Kika kamu da ulcer, since when?" "Bafa wani Abu bane tun Ina secondary ne Amma tunda aka fada min na rage cin wadannan abubuwan more especially da dare idan Zan kwanta saina daina ciwon cikin". Plate din ya ture gefe, "tashi ki Kai fridge ki dawo". Kallonsa tayi da alamar tambya "to Kai bazakaci ba" "Ni saboda ke na sawo coffee ko fruit kawai nake Sha a irin wannan time din, ki wanko Mana Apple kawai ya Isa". Saida ta wanko ta kawo sannan ta dauki kazar ta Kai fridge din ta dawo. A Dan nesa dashi ta zauna taga alamar 'ya abun nasa Yau suna kusa. Matsowa yayi jikinta da plate din Apple din Yana Danna waya da alama kamar Kira yakeyi Apple din ya Mika Mata Yana ci gaba da trying Kiran, sau biyu Yana Kira ba'a daga ba ya hakura ya aje wayar. "Labarin ki Zaki bani tun daga primary, secondary Zuwa Yau din Nan da muke tare Kuma ki fada min dalilin da yasa ake fasa aurenki da dukkan Wanda sukaso aurenki laifin na waye? Ok kafin Nan Bari na tambaye ki wani abu" Wata wayar ya Ciro daga aljihun gefen hagu na rigarsa. Jikinta ya matso sosai Kusan Rabin jikinsa Yana cikin nata ya kanainaye ta CCTV ya kunna ya Mika Mata ya saka fullscreen gurin gate din gidansu ne Mama da Asabe ta gani tun tsayuwar motarsu har zuwa gurin Mai gadi Saida ta gama ganin komai yace "Daman Kuna abin kirki da Mama ne? Kuma wacece wannan Dan yanzu da Daren Nan da naje yiwa su Ammah sallama naganta a dakin mamar kenan daga Nan can sukayi" Ya fada Yana tsareta da idanunsa masu razana ta. "A'a ni bana wani good term da Mama ko kadan Dan da sam ita da Aunty salma basa yina Daman Hameeda ce tawa idan tana gurin ba Wanda ya Isa ya Fadi marar Dadi a kaina, to ita dinma bansan meya canzata ba lokaci daya tayi min cin fuska ba ko Kara gani a tsaye, ita Kuma wannan Asabe ce aminiyar Mama ce komai tare sukeyi". "Ok ba damuwa". Wayarsa ce ta dauki wani slow music alamar shine ringtone din wayar, dauka yayi tare da sallama. Magana ya Fara Bai jira Wanda yayiwa sallamar ya amsa ba. "Kazo Azare katagum local government a cikin local government ne na Bauchi state ne a duba map zakaga inda location din yake amma kada ka biyo ta jos Nissan yayi yawa ka shigo ta Kano kawai karfe bakwan safe tayi maka a garin". Abinda ya fada kenan ya katse Kiran. Wani Kiran ya Karayi ringing daya aka dauka. "Bilya a canzawa Mai gadin gidana gurin aiki ya Koma Sharar compound din makarantar yaran Nan kawai" kit ya kashe Kiran duk tana binsa da ido. Agogon jikin wayarsa ta kalla Sha biyu da Rabi. A marairaice ta dube shi "yaushe zamu tafi nifa Ina Jin tsoron dare fa". Kansa ya kwantar a cinyarta Yana facing din face dinta. "A Nan zamu kwana bakiga harda jakar matafiya ba? jiranki nake ki bani labarin naki kinyi shiru kin shareni". Dan turo Baki tayi "Toni me zance maka ai kasan komai" "Kamar Yaya nasan komai, harda labarin da aka turo min ta msm na duk Wanda kikayi tare dashi Saida ya sanki 'ya mace yaji test din Bai Masa ba tunda kyawun iya jiki da fuska kawai ya tsaya" shima Hakan ne tunda anfada min?" "Cikin razana ta nuna kanta da hannu. "Ni Kuma Zina? Waye yayi min irin wannan tozarcin? Me nayi musu haka da zafi da har za'a yi min bita da kulli irin wannan?" Sai hawaye. "Ya Ilahiy!! Ken wace iri ce daga tambaya sai kuka kewai kuka baya da wahala a gurinki Kamar wata 'yar film, tab kice na iya bakina, idan na karanto Miki sauran yau ma a Asibiti zamu waye kinga the chapter is closed labarin ma a bar shi Gama Shan apple din ki kwanta Naga alamun barci a idonki Ni aiki Zan karasa". Cikin shashhsheka tace "basai nayi komai ba tunda banzo da kaya ba haka ma zan iya kwantawa". Luggage din ya nuna Mata da Hannun. "Ki bude akwai komai a ciki ya janyo laptop dinsa ya Fara aiki bai Kara bi ta Kanta ba, yayi biris da ita Kamar besan Allah yayi ruwan tsirarta a dakin ba. Nuku nukunta ta Gama sannan taje ta bude jakar kamar yanda ya fada kayansu ne ita harda sleeping dress Kusan uku Saida ta duba sosai sannan ta samu wata doguwar Riga Mai Dan dama dama ta dauka ta nufi toilet duk abinda take Yana kallonta ta gefen ido har ta shige. Ruwan zafi ta hada ta zuba turarikan wankan data gani a gurin ajiye, shigewa tayi ciki tayi kwance ruwan Yana ratsata kamar zatayi barci ta jima sosai sannan tayi wankan ta fito, sai da ta goge jikinta ta zura rigar barcin cotton ce mai laushi ta sauko Mata har Kusan gwiwa sai da matsalar ta dayi zif akayi Mata har kasa ga saman rigar wani net aka saka transparent komai a waje yake ba wani sirri Kai kawo da dinga yi a toilet din daga karshe towel na wanka babba ta rufo a jikinta ta fito. Dago ido yayi yana kallon ta sai Kuma ya janyesu yaci gaba da aikinsa cikin kware, idan yaci gaba da kallonta wlh wata dariya zata kubce Masa, shi dai yasan duk wayon Amarya sai an Sha manta. A darare tazo ta zauna a nesa dashi. " Ki tashi ki kwanta ya nuna Mata tsakiyar gadon. Jinjina Masa Kai tayi ta Haye tana Jan blanket din tana rufe jikinta. Kusan Rabin hankalinsa Yana Kanta Yana kallonta tayi Addu'ointa shafa a jiki, tun Tana Dan Jin dar a jikinta har barci yayi awon gaba da ita. Sai gurin daya ya kammala duk abinda ya kamata ace ya gama. Wanka yayo tare da alwala pyjamas ya saka masu kalar off-white sannan ya tada nafila raka'a hudu yayi ya sallame ya jima Yana addu'a kafin ya nufi gado dariya ta bashi blanket din daban ita daban sai barcinta takeyi cikin nutsuwa face dinta ya kurawa ido "yes she's beautiful" ya fada a hankali kamar Mai tsoron kada taji. Kusa da ita ya kwanta kamshi turarensa Dana turaren wanka sai suka bada wani kamshin Mai dadin shaka, madaurin jikin rigarsa ya since ya zare rigar daga jikinsa ya kwanta a jikinta Bata ko motsa ba a hankali ya saka hannunsa ya zuge zif din jikin rigarta yayi mamakin nauyin barcinta blanket din ya janyo ya lullubesu da shi sannan a hankali ya mannata da jikinsa yana sakin ajiyar zuciya, a cikin barci taji Kamar hannu na yawo a jikinta a Dan tsorace ta bude idonta ga dakin ba haske so sai, Sam saita kasa gane takamaiamai a Ina take ga ta Kuma a jikin mutum ko Riga Babu. "Wayyo Allah na!!!" ta fada jikinta ya dauki rawa.. "Shittt, cool down nine kiyi barcinki Nima barcin nakeji.. .✨✨ ✨✨ AUREN HUCE HAUSHI Page 28 ____Hankalin Zahra be kwanta ba sai da taji Yana maida numfashi a hankali alamun barcin ya dauke shi ajiyar zuciya ta sauke da farko Bata yarda ba da yace barci zasuyi Saida ta gani da gasken yayi barcin. Kokarin zame kanta da yayi Mata pillow da gefen kafadarsa tayi, a cikin barcin ya kara janyo ta jikinsa yana gyara Mata kwanciyar amman idonsa dai a rufe, shiru tayi lif a jikinsa Dan Bata son ya farka su hada ido ai da kunya amma taga alama shi bashi da ita misqalazarratin idan wani ne ai zuwa yanzu Basu wani sababa yanda abun yazo musu a hagunce, ko dan shifa yana ikirarin ya santa batun yanzu ba to a Ina?Kuma waye shi?daga Ina yake? Waye sameer a zahiri shi yaron sameer ne ita Kuma a bad'ini shi yake bashi directive abin da daure Kai Kuma yace ya manta garinsu da komai nasa Amma a gurinta yana fada Mata ya tuno kakarsa har da 'yar tsamar da sukeyi. Tunani barkatai ta dunga yi har barci yayi awon gaba da ita, karfe hudu da rabi na Asuba alarm din daya saita ya tashe su kusan lokaci daya suka farka har lokacin tana jikin shi, shiru tayi Bata nuna ta tashi ba, so take ya wuce toilet. Addu'ar tashi daga barci yayi a hankali ya zare ta daga jikinsa kura Mata Ido yayi a cikin dimligh din dakin face dinta sai glowing takeyi ko Ina a jikin fresh sai wani sansanyan kanshi ke fita daga jikinta wanda har ya zauna a jikinta Dan duk jikinsa kamshin yakeyi, light kiss ya Bata a kumatu ya gyara Mata rufar saboda sanyin AC ga sanyin Asuba. Duk abinda yake tana jinsa bakam tayi Dan ji tayi wani irin nauyinsa ya rufeta Wai wane irin barci ne tayi har yayi sabgar rabata da rigarta amman Wai Bata sani ba, Jin karar ruwa yasa tayi saurin tashi ta janyo rigarta tana cuno Baki. "Haka kawai duk a kalleka waya sani ma ko Abu ya saka a cikin Apple din Dana Sha shike Nan na Kama barcin asara sai yanda yayi Dani" da sauri ta ida janye blanket din tana duba jikinta Jin ba wani bakon Abu yasa taji sanyi a cikin ranta, sai Kuma abun ya Bata dariya, Jin ze fito yasa ta koma ta kwanta jallabiya ya zura ya saka tashi ka fiye naci, ya dauki tasbasha (counter( ya matso kusa da ita Dan guntun ruwan alwala na fuskarsa ya yarfa Mata kadan a fuskar ta. "Ki tashi kiyi alwala an kusa tada sallah nasan idonki biyu tun lokacin Dana tashi". Ya fada Yana nufar kofa zuwa masallacin cikin hotel din. Tashi tayi ta nufi toilet din a gurguje tayi wanka ta daro alwala lokacin data fito har an idar da sallar, lotion din data gani ta shafa ta bude jakar duk wani abun da zata bukata ya sako a ciki ita mamaki take to a Ina ya Sami kayan ita dai ba nata ya dauka ba, hatta bra ma size dinta ce doguwar Riga ta cire daga leda ta saka baka Mai aikin stone, hijab ta saka ta tada sallah. Har ta gama azkar Bai shigo ba sai gurin shida da rabi ya shigo directly inda take ya nufa. "Barka da Asuba". Zahra ta fada tana sadda Kai kasa, shiru yayi kamar Bai jita ba sake maiamaitawa tayi. "Taso kiga yanda ake gaida Dear ba irin wannan local gaisuwar ba" Sunne Kai tayi tana Dan murmushi, tsugunawa yayin daf da ita yana kallon 'yan yatsun Hannunta sumul sumul dasu kamar Bata aikin komai da Hannun, dagota yayi gaba dayan ta ya mannata a jikinsa "ji nakeyi kamar kada nayi tafiyar nan ko Kuma na daukeki mu tafi, idan na tuna zanyi nesa dake wlh wani irin rauni ne yake kamani naji kamar idan bana Nan wani Abu ze faru". Ya fada cikin muryar karaya da gaske a 'yan kwanakin Nan Yana Jin wani Abu daya fi na da a tare dashi. Cikin 'yar siririyar muryarta tace "ba komai kaje kawai Allah Yana tare damu ba abun da ze faru sai abinda ya hukunta a kaina, Allah ya bada nasara yasa a Dace, kawai dai Dan Allah kayi min wata alfarma kafin ka tafi". Hijabin ya zare a hankali daga kanta ya Dora a Kan bed side kafin ya zaunar da ita a jikinsa as usual. "Fadi wace bukata gareki". Dan shiru tayi kamar bazatayi magana ba. Oya fell free with me, kiyi magana Mana kinsan eight thirty nake so na wuce". "Daman so nake na ringa zuwa Dr.sulaimanu Adamu college of Hygiene inda nayi service na ringa yin lectures ko sau biyu ne a sati". Wani kallo yayi Mata na Amma Baki da lissafi. "Ni matata da yawon aiki? Gaskiya A'a! Wannan bukatar Bata karbu ba, me kikeci na baka na Zuba indai aiki ne wlh sai kin gaji da yinsa, tashi daga jikina kin wani samu cinya kin dane,kada na makara nayi missing flight mu tsuguna duk dan burin bawa ya rushe". "Yanzu Allah bazaka Bari na rinka Zuwa ba". Ta fada a marairaice. "Kinsan Allah wlh Zan hadaki da zayyan Dan nasan Yana daf da shigowa garin Nan ya juya min dake can kauye gurin Hajiya Inna ko banza kin tuka mata tuwon dawa kin mata shara, kinga ita gaba ta kaita balarabiya na mata aikatau ita kuwa bakar fata Kinga sai mu Dora a media muma 9ja munci gaba ana zuwa daga middle East ana Mana aikatau". Ya karasa fada Yana Jan Dan tsinin Karan hancinta. Tana kokarin magana wayarsa dake Kan bedside ta dauki wani kidan larabawa Mai dadi. "Dauko min wayata Dan tsabar na Zama mijin ......, Gashi Nan ringtone din ma kidan kune na saka". Wayar ta dauko, Zayyan ta gani kwalalo idanu tayi Ashe da gaske yake da yace Shi wannan din zezo yanzu ko waye shi kuma "oho" ta fada a zuciyarta. Wayar ta Mika masa. "Ka karaso?" Abinda taji ya fada kenan Bata San me yace Masa ba taji yace "ok, ka shigo ciki akwai securities a kofa zasu zasu rakoka gurin da Zan ganka". Ya kashe Kiran Yana nufar kofa, ki shirya kafin na dawo yanzu zamu wuce". Yayi Gaga abinsa ya barta da Baki a sake "ikon Allah shi Kuma ko waye yake bada umarni cikin dare ya wayi gari da abinda ya bukata tasan ko waye daga nesa yake Dan jiya tanaji Yana fadin kada a biyo ta jos a biyo ta kano, ita duk ya Gama Dame Mata lissafi wlh. ****** A hankali yake tafiyar cikin nutsuwa Amma da gani kasan tafiyar ta ingarman namiji ce, tunda ya doso gurin Zayyan ya kafe shi da ido, take ya shiga jinjina lamarin ogan nasa wato ana zaton wuta a maqera said gata a masaqa, waze tab'a tunanin sa a irin nan yayi masifar bada kafa. Bai Farga ya kureshi da ido ba Saida yazo daf dashi, "sorry sir" ya fada Yana sadda kai, baiyi magana ba ya mika Masa hannu wannan d'abi'ar sa ce baka Masa irin gaisawar Nan sai dai kuyi musabihwa. "Barka da Asuba ya Hanya?". "Alhamdulillahi." Ya fada sai da Mahmud ya zauna kafin Zayyan Shima ya koma ya zauna. Kamar bazece komai ba gurin ya dauki shiru. Saida yaja fasali sannan yace. "I hope ba Wanda ka fadawa munyi waya ga Kuma inda zaka sameni?" Kai ya girgaiza "ko daya oga ba Wanda yasan inda na tafi kawai nace musu zanje gida ne na samu Kiran gaggawa". "Good, na kiraka ne zaka zauna gidan da wife Dina take zanyi tafiya, Wanda na saka gadin Naga alamar gaskiya Bata isheshi ba, ko Kuma ze iya komai saboda kudi, zan turo maka pictures na wasu Mata koda Wasa kada kabar kafarsu ta shigar min gida shi yasa na taso ka da tsohon dare ". Zayyan jin magwnar yayi wani banbarakwai "wife Kuma? To ta ina Hakan ta faru? mutumin da ake tunanin baya kasa sai Kuma ya ganshi a nan Yana wata irin rayuwa hankalinsa kwance, ga abubuwan tambaya Amma ba Halin yinta. "To in Sha Allah baza'a samu matsala ba". "Yanzu zaka shiga cikin Ibrahim ze nuna maka dakin da zaka huta daga Nan zuwa sha daya Binyaminu ze shigo kuje gidan". Ya fada Yana mikewa. Da kallo zayyan ya bishi har ya b'acewa ganinsa, ajiyar zuciya ya sauke Yana jinjina Lamarin ogan nasu wato duk yanda kasan Shi idan yayi wata bada Qafar saika rasa gane wace alkiblar ya kalla. "Wife Dina". Yanda yayi maganar kasan ba wasa cikin Yana wannan tunanin Ibrahim ya karaso Bai sani ba. Da azama ya shiga falon a zaune ya sameta da luggage dinsa a kusa da ita tayi rolling da Veil din rigar sai tayi masa wani irin kyau, a slow ya karasa inda take zaune ya saka hannu ya dagota tsaye ya sumbaci saman goshinta. "Nayi Miki irin gaisawar ku, Ina key din lokaci Yana ja kada da gaske nayi sakaci kija Mana, muna lallabawa, kin hakura da Zuwa makarantar naji Baki ce komai ba?" "Bani da say, sai yanda kace haka za'ayi". "Nace A'a! in dai Ina raye da lafiya ta bazaki nemi komai ki rasa ba Koda kuwa faskare zanyi to zanyi na samu abinda zankula dake".ya fada Yana daukar luggage din ita Kuma ta nufi kan fridge inda ya ajiye key din jiya. A jere suke tafiya sunyi wani irin dacewa wadda dole idan ka kallesu ka qara suna kokarin fita daga reception su Zayyan suna kokarin shiga, Mahmud ya kalla da jakar matafiya a hannu Yana rike da Hannun Zahra,. "Kam bala'i" Yaji Bakinsa ya subuce ya fada Yana matsawa baya Kamar yanda Ibrahim yayi. "A sauka lfy" Ibrahim din ya fada shi kuwa Zayyan kamar an saka makulli an datse Masa baki. "Ka bashi key din dakin ka biyoni mota Zan baka sako". Ya fada Yana duban Ibrahim, mota Zahra ta shige ta barsu suna tattaunawa kafin ya shigo ya tada motar ya nufi get din fita har yabar harabar hotel din, Zayyan na lekensa ta window sai dai yasan idan yayi magqnar Nan da wani kwabarsa ce zatayi ruwa daya fesa labari, oga da rije jikar mace uwa uba yana tukata da kansa Kai wannan abin surprised da yawa yake"Ga bikin zuwa ne babu zani. Tafiya yake da hanzari Dan ma safiya ce sosai titin ba yawan jama'a cikin Kan kanin lokaci suka shigo unguwar, Horn ya danna da karfi da gudu Mai gadin yazo ya bude yana fadin "barka da zuwa!" Da gudu ya Koma ya dauko sakon dasu mama suka kawo jiya Yana fadin "barka da Asuba yallabai gashi jiya bayan futarku su Hajiya Babba sukazo suka bada a ajewa Hajiya". Ya fad'a Yana risinawa Yana mikawa Mahmud ledar. Saida ya karewa shi da ledar kallo, sannan ya hade gabas da yamma yace ka rika idan kana so, Kuma Ka hade kayanka in anjima kadan binyaminu ze zo da Wanda ze canjeka aikin Nan adalci daya nayi maka ban koreka ba zaka koma share-sharen makarantar Yara kawai". Jiki na tsuma Mai gadi ya durgusa Yana fadin "Yallabai me nayi haka da zafi Dan Allah kayi hakuri wlh baza'a qara ba ka rufa min asiri". "Iya Alfarmar kenan bana korar ma'aikaci sai lefinsa ya Kai uku to Kai daya kayi ba tare da kasan laifi bane shi yasa nayi maka uzuri bazan rabaka da rufin asirinka ba dauki kaje yanzu Zan fito". Jiki ba kwari ya dauki ledar ya juya Yana ta faman tunanin ta ina ya kuskuro yallabai jiya lafiya kalau suka rabu yau Kuma ya tashi da canjin gurin aiki da Allah ma ya dube shi da Rahama daba Kora bace days shiga uku. Suna shiga Mahmud yayi bed room dinsa ita Kuma ta nufi kitchen ta Fara hada abu marar wahala coffee ta dafa Masa sai sandwich kawai tayi shaf-shaf a tray ta Dora direct bedroom dinsa ta nufa ya fito daga wanka Yana goge jikinsa a ranta tace shi baya mura any time wanka kamar dangin kwadi. Sallamar ta ya amsa Yana aje towel din dake hannunsa. "Ke! Me kikayi daga zuwan mu ba dai abinci bane ko? Ni bana cin komai a irin wannan lokacin". Langabe Kai tayi tana dubansa kasa-kasa har Zuwa lokacin wani nauyinsa takeji. Yana ankare da ita. "Coffee ne fa da sandwich nayi maka Dan Allah kada ka tafi da yunwa,alhalin gani a tare da Kai ai da naji kunya daga zuwa ka nemi abinci a kanon". "Inye ashe dai ana son mamudan?". Ya fada yana nufar inda ya aje kayan da ze saka kananun Kaya ne na kamfanin Armani ya saka bako kunya ya cire rigar wankan ya tsaya daga shi sai boxer short, da sauri ta runtse idonta Dan Bata zata zeyi irin wannan abunba Yana kallonta ya basar yaci gaba da shiryawarsa, Zama yayi Kan sofa Yana umartarta ta kawo masa coffee din nan duka ta dauko ta aje gefensa ya dauka Yana sipping Yana kallonta tana Wasa da gefen veil dinta da ya sauko, sandwich din daya yaci ya yaji ya isheshi Shima Dan kada ya watsa mata kasa a ido ne, amma Sam baya iya cin komai a irin wannan lokacin. "Zauna muyi magana" ya fada Yana dubanta,.gefen sofar tayi niyyar Zama ya tikota "Kinga gurin zamanki Nan ya dorata inda ya Saba.. "Zan tafi Baki San cikakken asalina ba, Zan fada Miki saboda sha'anin Rai da rayuwa kona dawo ko ba na dawo ba, Ni haifaffan garin sokoto ne iyayena duka biyun sunan Nan ni dangatan iyayena ne da kakata Hajiya Inna, suna Sona yanda Baki zato yanayin rayuwa ne ya kawoni nan, duk family na ba Wanda na fadawa labarinki sai kakata ta sanki a hoto tasan wasu labaranki, kota Allah ta kasance wannan dana Kira ya zauna yayi min gadinki sunansa zayyan na fada Masa ke matata ce ze sadaki da Family na, Dan Allah kiyi min Alkawarin duk rintsi bazaki juya min Bata ba, ki rike min aurena da Kima da daraja, idan Allah yasa na dawo Zan fada Miki koni waye da duk abinda ya shafeni na rayuwata Daman taki na sani ba sai kin fada min ba, duk abinda kike bukata ki duba waccen lokar akwai kudi a ciki bangaren abinci Kuma nabar komai a Hannun Habib, ga Kuma kudin da Sameer ya Baki ban Baki ba". Ya aje mata su a akan cinyar ta. Jin tayi shiru yasa ya dago fuakarta da hannunsa,kukan Zuci take ba wani sound sai dai hawaye"subhanallahi kuka dai? Kona fasa tafiyar nan kawai tunda Naga hankalinki yaki kwanciya da ita" "Ba komai kaje kawai naji Kanata nanata maganar in baka dawo ba na sani ko idan ka tafi bazaka dawon ba". Lakuce Mata Baki yayi "ai kece bazan dawo din ba, wannan ya shafa cikinta sai kin ajiye Mana babies a ciki idan naki dawowa aini nayiwa kaina, ki kwantar da hankalin ki nema zani ki min addu'ar samun nasara". ✨✨✨ ✨✨✨ AUREN HUCE HAUSHI Strory & Written By Maman Fateemah Page 29 📖🖋️ _____ Sun jima a haka Yana lallashinta kafin ya dagota su tashi tsaye tare " me za'a bani nayi guzuri dashi?" Ya tambaye ta, shiru tayi kafin ta Dan watsa hannu tana Dan kallonsa ta gefen ido. "Ai kaga bamu kwana a gidan ba bare nayi maka wani Abu Saida idan biscuits din Nan Zan dauko maka sai ka tafi dasu na bada a sawo min wani". Dariya abin ya bashi ita bilhaqqi da gaske take fada Wai biscuits kamar wani yaro. "A'a niba shi nake so ba tsarabar da zan rike Ina tunawa da ita har na dawo". "Me Kenan?" Ta tambaye shi cikin nuna rashin sani. Jikinta ya matso sosai ya riko ta Yana kallonta da wani yanayi mai wuyar fassarawa, Bakinsa ya Kai Kan nata Dan bakin yasa Hannun ya talkafo kanta batayi zato ba tsammani taji harshensa na yawo cikin bakinta ya lalubo nata harshen cikin gentle yake tafiyar da ita ba kamar ranar nan ba, sun dauko Kusan minti biyar Yana Abu daya ji tayi kafafunta na neman gagarar daukar ta, jin jikinta na rawa yasa ya Kara mannata da jikinsa wani Nishi tayi ba Halin magana, kokarin yanye harshenta take daga Bakinsa Kai ya girgaiza Mata sai da yayi mai isarsa ya saurara Mata Kan gadonsa ta zube da gaske ya kashe Mata jiki ji take idan ta taka kafarta faduwa zatayi. Dan rankwafawa yayi saitin fuskar ta "Haba 'yan Mata be strong Mana me akayi da maza inji karya, taso muje ki rakani idan na biye Miki labarin salo ze canza". Ya kamo hannunta ya mikar da ita, jakar laptop dinsa kawai taga ya dauka, gyalenta wanda yake yashe a kasa ya tsuguna ya dauko Mata Yana rufa Mata a kanta. "Zaki bani Aron motar ki naje Kano da ita? amma fa saina dawo na dawo Miki da ita a airport Zan bada ajiyarta yanda idan muka dawo saina karba kawai". Kai ta gyada Masa alamar Eh. *A'a magana zakiyi idan kin amince to idan Baki amince ba na nemi hanyar Tasha kawai". "Ka dauka kaje da itan koka dawo ma na bar maka za'a kawo min wata ba kaji Abba ya fada ba". "Ke! Kinsan kudin ta kuwa zakice kin barmin Dan ki hau Abba ya saya Miki, Aron ma Ina laifi". Yaja hannun ta suka nufi kofar a falo ya tsaya Yana wasu 'yan dube duben da Batasan Kona menene ba sannan suka nufi harabar gidan, kasa hakuri tayi ta jefa Masa tambayar. "Wai haka zaka tafi ba kayan sakawa da takalma da sauran abun bukatu ne?" Dan shafa gefen fuskar sa yayi ya Dan furzar da iska daga Bakinsa. "Bana tafiya da Kaya ai wahala ce nasan duk inda zani akwai na sayarwa na saya kawai, aikin gane?"kallonsa kawai batace Masa komai ba. Saida yaje gurin Mai gadi ya bashi wata envelope sukayi maganganu sannan ya dawo gurin da take tsaye. "Zan tafi sai Allah ya dawo Dani, ki kula da kanki bana son yawo Amma idan gidan Ammah ne ko Aunty Hasana idan Bata koma Jos ba kina iya Zuwa". "To na gode, Allah ya tsare hanya ya bada sa'ar abinda akaje nema". "Allahumma Amin. Allah ya tsare min ke daga sharrin mutum da Aljani da dukkan abinda yake cutarwa, ya Ubangiji na bar maka amanar iyalina ka Zama gatan mu". Ya fada yana nufar motar, a hankali ta biyo shi ya bude ze shiga ta riko hannunsa ta Manna masa kiss a tsakiyar hannun. "Safe journey" ta fada da wata murya Mai rauni da gudu ta juya idonta fal hawaye. Tsaye yayi Yana kallon ta har ta shige ciki, ajiyar zuciya ya sauke kafin ya shiga ya tada motar jikin window ta tsaya har Saida ya fice daga gidan. ________________________ Tunda Mahmud ya bar cikin gari ya saki motar, rabon da yayi tuqi irin wannan har ya manta, kyakykyawar awa daya da minti arba'in da Tara ta kawo shi Kano, daga Hotoro NNPC sai ya shiga ta ring road ya fita 'yan kaba haka ya dunga yayyankewa har Zuwa round about na sani Baban kwari Sannan ya nufi Malam Aminu Kano international airport,Yana daf da shiga gate din ya saka face mask da glass sannan ya shiga, wayar Sameer ya Kira tana daf da katsewa ya daga. "Kana Ina? Na shigo yanzu ina fatan komai ya dai-daita?". Dan Jim ya yi yana sauraren sa. "Ok kazo ina parking lot inda ake bada ajiyar motoci". Ya sauke wayar Yana kalon masu Kai da kawowa. Yana Nan tsaye har sameer din ya karaso ya gaishe da Mahmud cikin girmamawa, jakar laptop din Sameer ya karba da key din motar ya nufi inda suke da alhakin karbar ajiyar, shi Kuma Mahmud ya nufi reception din. Sameer Bai jima ba ya dawo da takarda shedar bada ajiya, sun Dan tattauna kafin lokacin tashinsu yayi, zasu shiga screening ne Mahmud ya Kira wayar zahra, tana kwance a gado rungume da pillow bayan tayi kukanta Mai isarta ta lallashi kanta tunda Babu Mai lallashin gani takeyi shima kamar ya tafi kenan. Ringing din waya taji da sauri ta tashi Dan ita Sam tama manta da wata waya tunda ya Bata Bata karabi takanta ba, da sauri ta dauko tana duba waye ya Kira MM DANGE ta gani wani sanyi taji ya saukar mata, Picking tayi tare da sallama, sai kuma tayi shiru. "Zamu tafi ne nace bari na kira na fada Miki, ko zamu sake waya ze iya kaiwa jibi kada hankalinki ya tashi idan komai ya dai-daita Zan kiraki in Sha Allah". "Tom Allah ya saukeku lfy". "Allahumma Amin my precious, please take care bye". Ya katse Kiran yasan idan yaci gaba kuka zata saka Masa ya rasa wane irin idanu gareta masu saurin kuka. Sha biyu da rabi jirginsu na kamfanin air Max ya daga. Wayar tabi da kallo kafin ta aje kusa da ita, sai Kuma ta tashi kamar wadda aka zabura. Wayar ta dauko dubawa tayi wata baguwar number ta gani batayi kasa a gwiwa ba tabi Kiran Dan missed call ne tunna jiya. Cikin kankanin lokaci Kiran ya shiga Bata jima Tana ringing ba aka daga muryar matashiyar macece daga ji tana ji da ajinta sallama Zahra tayi Mata suka gaisa sannan zahrar tace Mata taga missed call dinta ne a wayar ta. "Missed call Dina gaskiya bani na Kira ba Amma Dan Allah wacece ke?. Yar dariya Zahra tayi kafin tace "sunana Fatima Zahra Muhd sani Ni mazauniyar Azare ce ta jihar Bauchi". Kit ta kashe wayar ta yunkura ta tashi, ta nufi kofa tana daf da fita taji wayar ta Kara daukar Kara ta dawo number dazu ce yi tayi kamar zata share sai Kuma ta dauka taji me zata fada Mata. Sallama tayi daga can ta amsa sannan ta Dora da fadin "Dan Allah kiyi hakuri da farko ban ganeki bane sai da Kika fada min sunan ki wlh nice na Kira bansan yanda akayi banyi saving number din ba matar oga Mahmud ko?" "Eh nice ke wacece?" "Sunana Fateeha matar Sameer Babban yaron oga jiya ne ya bani number yace na kiraki na gaisheka nayi Miki Allah Sanya Alkhairi sai Kuma ba'a daga ba, an Sha sauga bamuzo mukaga daki ba gashi har sun wuce China, amma in sha Allah idan suka dawo zamuzo indai ban haihu ba har lokacin" "Nagode kwarai da gaske,Amma naji kince China ba UK zasu Fara Zuwa ba? To can din zasu tunda kune masu tafiyar Amma na dauka da China zasu Fara tunda canne aka samu matsala sai Kuma Dubai, kinsan ogan naki ne kamar computer yake baya gajiya da aiki danma yayi wannan hutun Mai yawa sai Habibi ne yake wasu ayyukan". "Hakane kam aiya huta yanzu sai a Dora daga inda aka tsaya". "Ai gaskiya samun kamar oga Mahmud sai an tona". Basu jima ba sukayi sallama. Ta Dade a zaune tana jujjuya hirar su da matar Sameer, zamewa tayi ta kwanta tana duban sama a hankali ta furta. "Ubangji ga baiwar Mai rauni ka jibinci lamarina Kasan ko waye ka hadani dashi ka Kuma sakamin nutsu a tare dashi ban tabaji bana sonsa ba Amma lamarinsa Yana bani tsora na rasa alkiblar daya duba, Allah ka Zama gata na ka jibinci dukkan lamurana Dan Isar Manzon Allah s .a.w.w. Tashi tayi ta fita dakin nasa ta koma dauko tray din da Takai Masa break fast, duk wani Abu daya danganci kayan electronic sai ta kashe sannan ta fito tana gangarowa daga steps din corridor ne taji door bell din tana Kara alamar anyi Baki, a Kan dining table ta aje kayan ta gyara gyalenta ta nufi kofar. Budewa tayi sai sukayi arba da zilai Mai aiki da 'yar jakar kayanta. Cikin farin ciki Zahra ta karbi jikar kayan tana fadin "sannu da zuwa anti zilai".. Suka shige ciki murnar Zahra taki boyuwa itama zilan ba Karamin murna tayi ba lokacin da Ammah ta fada Mata zata zo ta Taya Zahrar Zama. Nan suka shantake suna Hira har Kusan karfe dayan Rana kafin Zahra ta raka zilai dayan dakin da ba cikinsa take ba ta aje kayan ta. Tambayar Zahra zilan tayi me zata dafa musu, "Ki dafa komai na ni harna manta wlh ashe ko break banyi ba, ga sandwich can ki dauka kada ya lalace, Zan shiga na Dan kwanta kafin karfe biyu" "To Allah kaimu" zahra tace "Amin"harta fara tafiya zilan Kira sunan ta tsayawa tayi har zilan ta karaso. "Uwar dakina Naga kamar wani mutum mun gaisa dashi ko Mai gadi kuka canza". ,"Eh Mai gidan ne ya canza shi wlh jiya lfy muka fita Amma yau muna dawowa ya sallame shi, wani ya Kira ya zauna Dani kafin ya dawo. "Wani Kuma daga Ina,?. "Nima ban san daga Ina yazo ba" Tab Allah kyauta ya kamata asan asalinsa gaskiya zamanin ne yazo da wata irin rayuwa sai godiyar Allah". "Wannan gaskiya ne". zahrar ta fad'a. Ita nufi bed room ita kuma zilan tana nufar kitchen. ✨✨✨ ✨✨✨ AUREN HUCE HAUSHI. Story & Written By Maman Fateemah. This page is deducte to the Family of late Alhaji Isah Musa bakin kasuwa kazaure. Innalilllahi wa Inna ilaihi raji'un! Ina Mika sakon jaje da ta'aziyya ga jama'ar garin MAJIA TAURA LG bisa ibtila'in daya samesu na gobara Mai Muni sakamakon faduwar tankar man petrol, Wanda yayi sanadiyyar rasa daruruwan rayuka Allah ya jikan wadanda suka rasu,wadanda Kuma suke gadajen Asibiti Allah ya tashi kafadunsu ya Basu lafiya yasa ya zamar musu kaffara ya kiyaye faruwar haka a gaba dan darajar manzon Allah s.a.w.w Page 30 _______Misalin karfe daya da rabi Mai a dai daita sahu ya sauke Asabe a bakin gate din gidan Zahra Dan yauma Saida taje can kauyen jama'are gurin wani mutum da wata kawarta ta tab'a fada mata shi, Nan ma ta karbo abubuwa Wanda za'a binna a gidan Wanda har abada Mahmud baze kara waiwayo garin Azare ba ko sunan jihar Bauchi ma Sai yaji ya tsane shi. Cikin karfin gwiwa ta karaso bayan ta sallami Mai Dan sahun tunda tasan Mai gadin Dan hannu ne dubu biyu ta Isa tasa yayi musu kowa ne irin aiki ne, iyakar ta tace masa na tsarin gida ne ze binna Mata saboda yau da gobe. Knocking tayi da Dan karfi tana mazurai ita ga uwar matar gida. Cikin takunsa na kakkarfa ya bude kofar gate Dan da hanzari tayi baya Dan ji yayi Kamar ze bangaje ta, kallo daya yayi Mata ya gane face din Dan hoton da oga ya nuna Masa yafi bada mahimmanci akanta Dan ita ce suspect dinsa ta farko, yasan da ita za'a yi amfani gurin isar da ko wane irin sako ne. Da hargagi Zayyan ya tunkaro ta. "Wa kike nema?" Duk daburcewa tayi nan da Nan jikinta ya dauki rawa. A'a Daman gurin matar gidan nazo munzo jiya ne basa Nan shine na dawo yau". Ta fada tana rawar murya. "Kama gabanki Nan ba wata mace a ciki gidan maza ne, idan Kuma Zaki shiga Bismillah tsuntsu daga sama gasashshe, Dan muna da kudajen da basa haram akan duk Mai tsautsayi, idan na Kara ganin giccinki a wurin Nan saina hadaki da karena yayi min fata-fata dake, wuceeee min daga nan" yayo kanta,da gudu ta kwasa ko waiwaye babu. "Stupid! Da gani wannan tsohuwar kwarkwar ce wlh Banda oga ya hana da kinci na jaki banza wato kin samu oga a araha shine kuka Neman zaku masa shegantaka akan matarsa ni na rasa yanda akayi ma oga ya Fado garin Nan,? Kuma har ya iya Zama a haka ba wani damuwa, ko Dan meze dameshi Yana tare da wannan danyan gold din". Ya fada Yana komawa bakin aikinsa Amma zuciyarsa fal tunanin abinda ogan nasa ya sani game da wannan matan daya turo Masa hutunan su ya Kuma shata musu dogon layi. Asabe Bata samu zarafin tsayawa ba Saida ta dangana da wani gurin me suyar kifi a bakin titi shima gani tayi gurin da jama'a ko cimmata yayi za'a ceceta, gefe ta koma tana mayar da numfashi sai lokacin ta dubi hanyar data fito ko Mai Kama dashi Babu. Gefen wani dutse ta zauna tana tunanin to koba gidan da sukaje jiyan bane tunda ba wannan basamuden suka tarar ba Amma daga Daren jiya Zuwa yau har lamarin ya canza ita damuwarta daya shin sakon da suka bayar ya sameta ko kuma na jiyan ba shine asalin Mai gadin ba yayi musu ta 'yan duniya ya barbe kayan da kudin ya wuce nasa gurin. Tashi tayi Kamar wadda aka tsikara ta dauki 'yar ledar data sawowa Mai gadin Dan abun tohiyyar Baki sai Kuma labarin ya canza salo. Harta dauko wayar ta Sai ta mayar idan tayi gigin fadawa Mama kwabarta zatayi ruwa Dan a yauma Saida Mana ta karo kudi masu nauyi tace a bawa Mai gadin yanda duk abinda za'a saka shi yaji baze iya gardama ba, to idan ta koma Mata da wannan labarin amshe kudin zatayi tasan halinta kayan ta, data Bata naira dubu gara ta bawa Dan tsubbu dubu hamsin, Sam Bata karuwa da ita saita wadannan hanyoyin idan ta aiketa tunda itace amintacciyarta ta Nan takeyin nata duk rintsi bazata so ta rasa wannan mafakar ba Dan Kusan da ita ta dogara gurin kwaramniyar yau da Kullum nata. ******* Saida Zahra tayi barci Mai isarta sannan ta farka lokacin biyu har da minti ashirin da hudu, da sauri ta Mike tana addu'ar tashi daga barci tayi mamaki ita fa gani tayi kamar barcin minti goma Sha biyar tayi Ashe lokacin ya ja haka, alwala tayi tazo ta Fara sallah bayan ta idar wayar ta da dauko Ummee ta Kira cikin shauki tun dazu ta nemeta network din na garin ba kyau sai hakura tayi, Bata jima ba tana ringing aka daga ba Ummeen bace wata ce ta daga tana ta yi Mata larabcin gargal ita kuwa zahrar na language yafi kwarewa a Dan daburce tayi Mata bayini ta gane Ummeen ta fita masallacin Annabi sallah tunda har lokacin suna Madina basu tafi ba Kuma a yanda sukayi daga Saudi Arabia Nigeria zasuyo gurinta, sallama tayi wa matar ta kashe. Number sajida ta lalubo ta syprus tasan zata Sha mita tun ranar da sukayi ways da wayar Amatu tayi Mata buyagi ta kashe Basu Kara waya ba, har tayi ringing ta katse Bata dauka ba, Bata hakura ba wani Kiran ta karayi shima Yana daf da ze katse aka daga. "Haba bestie Ina ta kira kin shareni ko har yanzu fishin ne?" Mai makon taji bestien sai muryar Fatima taji tana kwallawa Sajidar kira tana fadin "ku taho ga Amarya Zahra! Zahra" ta kirata da karfi tana murna kamar zata tsaga wayar, daya bayan daya suka dunga gaisawa suna ta korafin amarci Dadi ta Kama waya ta rufe wato Bata so a shigar musu rayuwa ko? Hakuri ta Basu tare da fada musu tayi missing din waccen wayar ne har sim din, sai daga karshe sajida ta karbi wayar. "'yar duniya wato kinji dadin lamarin ko Kika wani shareni, ni yanzu ai yallabai Mahmud ya fiki kirki kinsan ya kirani Kusan sau uku? Daman ko Baki kirani ba Zan kiraki dazu wurin Sha daya ya kirani Wai na kiraki na lallasheki yayi tafiya ya baroki kina kuka?". Ya fada tana kunshe dariyar ta. "Malama ki fito kiyi dariyar ki sosai kada ta kume Miki a ciki,da kike wani kunsheta". Dariyar tayi da gasken sai tayi Mai isarta tace. "Dan Allah bestie mekika bawa wannan guy din Kinga yanda yayi masifar macewa a Kanki? Wlh har tausayi yake bani Ni har mamaki nake idan ya kirani Yana min maganarki ranar Nan fa cewa yayi na bashi labarin zamanki a Nan syprus din wlh nayi zaton da Wasa yaki tunda nasan ba Karamin cajin kudi za'ayi ba. Amma haka na ware na rinka bashi labarin har na Gama ko a jikinsa, yanzu Ina aka tsaya da fatan komai ya dai daita? Dan nafi son dai dai lokacin ganawarmu muyi murna biyu graduation da naming ceremony". "Wlh Zan kashe yaushe Kika zama haka Mai bin kwakwkwafin jama'a? to bazakiji ba an fada Miki kowa ma irinki ne ai wlh ya Abdul Hakeem ya debo ruwan dafa kansa Dan nasan Dan bawan Allah saiya rinqa guduwa daga gidan" Wata irin dariya ta saki tana fadin "billahil Azeem gara wata wainar data wake yarinya gyara zancen ki idan ana cin baure ba'a tona cikinsa Kuma idan ana sallah ba'a magana". "Wlh sharri zakiyi Masa Amma shi dai salihi ne". "A inda salihai sukayi karanci ba". "Mubar zance kawai tunda abun ya Zama haka". Zahra ta fada tana cire hijabinta daga jikinta vest ce Fara Kal sai wando shima fari ai pink din kananun flowers gashin tayi parking a tsakiyar Kan ta kashe da band shima pink, sai fito baby sak. Gyara kwanciya tayi, tayi ringinnine da wayar a kunnenta Hira sukaci gaba da sajida yawanci duk akan auren zahrar ne. Sun dauki lokaci Mai Dan tsawo suna tattaunawa akan bututuwa da dama kafin suyi sallama, ta nufi toilet wanka take son yi kafin ta fita cin abinci. ******** Jirginsu Mahmud a Addis Ababa Bole international airport yayi landing, daki biyu Sameer ya kama musu Nan kusa da airport din tunda a kalla zasuyi Kusan three hours. Saida ya kaiwa Mahmud jakar laptop dinsa sannan ya nufi nasa dakin, bayan fitar Sameer Mahmud wanka yayi sannan yayi sallah maimakon ya kwanta ya Dan huta sai kawai ya bude wayarsa so yake ya ganta duk wani matsi da yayi tana manne da zuciyarsa so yake ya ganta kafin ya kirata. CCTV ya shiga ta wayarsa duk abinda akeyi ya rinka bi Yana gani yasha dariyar karon Zayyan da wannan matar wadda ko sunanta Bai sani ba, shi yasa ya dauko shi yasan shi kadai ne cikin amuntattunsa Wanda ze Masa wanna aikin ba tare da an samu matsala ba. Saida ya gama kallon ko ina na gidan yaga ba wata matsala, sannan yayi zooming din cikin bed room dinta daga ita sai vest purple da wando skintight kanta tayi parking da purple din band sai tayi wani irin kyau na musamman, kura Mata ido yayi Kamar ya warto ta yakeji, turare ta dauko tana fesawa a jikinta. Nan ya shiriri ce Yana kallonta knocking din da akayi Masa ya katse Masa abinda yakeyi, umarni ya bada a shigo Sameer ne sai ma'aikaciyar hotel din dauke da tray na abinci sai karairaya take shi har dariya abin nata ya bashi, me Kamar zahra yaushe irin wadannan zasu burge shi, bayan ta wuce ne ya dago ya dubi Sameer "kada ka qara zuwar min da irin wannan a rinqa bawa maza suna kawo min kawai". "Noted sir" Ledar dake hannunsa ya Mika Masa Mai tambarin wani boutique ne, sannan ya aje Laptop dinsa a kusa dashi Yana nuna masa wasu ayyukan da ya Gama yanzu, sun jima suna aikin kafin sameer ya fita saboda lokacin tashinsu ya kusa cika shi kuma Mahmud ya ciro kayan da nufin sakawa. Saida Zahra ta Gama feffesa turarenta sannan ta dauko after dress ta zura ta yane kanta da gyalen sannan ta nufo parlour, zalai ta samu tana 'yan goge goge duk da ba wani datti a gurin, gaishe da zilan tayi tana Mata sannu, ajiye mofar tayi "Allah ya taimaki uwar dakina ga abincin can nayi Miki abinda kikeso faten dankalin turawa da pepper soup din kifi" Zama Zahra tayi tana fadin "Kai Amma wlh na gode kwarai da gaske shi yasa nake yinki kinsa favorite Dina wlh". "Ai shi yasa na cewa Ammah kada a wani dauko yarinya tun daga Mubi Nima na isa na zauna dake saina kirawo Kanwata Alawiyya ta cigaba da yiwa Ammar kafin Allah yasa yallaban ya dawo, ai ni har zaman wanka ni zanyi Miki Koda kuwa bakwa garin Nan ne". Dan smile tayi kawai bata ce komai ba saima ta canza akalar zancen. "Ni Kuma Aunty zilai kin mikawa mutumin Nan abinci kuwa?". "Ai tunda na Gama na zuba na hada harda ruwa da lemo na mika Masa. Naga Dan gayu ne beyi kalar masu gadi ba". Dariya zahra tayi tana fadin "Aunty zilai kenan shi Mai gadi har Kama gareshi". Yana da kama Mana Wai Kinga wannan din?" Na ga wani dai dazu ban sani ko shine Wanda aka Kira jiya cikin dare". " Cikin dare Kuma?" Kai ta gyada "Mata kusan Hakan tunda Sha biyu ta wuce ya kirawo wani kawai umarni ya bashi yazo garin Nan da safe kinsan bakwai a Nan tayi mass nifa mutumin Nan wlh tsoro yake bani na kasa gane kansa". Dan murmushi zilan tayi tana kallon Zahra "kiyi hakuri uwar dakina a hankali Zaki San komai a kansa badai Kuna tare ba da sannu Zaki gane shi din waye, kici abincin sai muci gaba da hirar idan kin gwma". Bata k'i Shawarar zilan ba ta tashi ta nufi dining ita Kuma zilan ta nufi dauko Mata ruwa da mutuniyarta farm fresh, sai da ta Gama cin abincin sannan ta dawo parlourn gurin da tabar Aunty zilan sukaci gaba da hirar su, amma Kusan hankalin Zahra yana Kan Mahmud haka Nan sai taji ya fado Mata ta yarda da ake cewa sabo turken Wawa, yanzu da baya Nan sai taji duk kewarsa ta kamata, tun dazu take duba waya ko zataga kiransa Amma shiru tasan tsakanin Nigeria da inda zasu indai da gaske chinan zasu da nisa a kalla jirgin zeyi landing a Ethiopia da India yaci ace ya kirata Amma shiru har Yanzu ko lfy? ta ayyana a cikin zuciyar ta. Ganin tunanin Zahra yayi zurfi yasa zilan ta tashi tana fadin Bari nayi wanke wanke tunda kin Gama da kwanukan" Tayi hanyar kitchen, ita kuma ganin tunanin ze dameta yasa ta kunna tv ta kamo MBC MAX tana son finafinan su sosai,Aunty zilan ma data Gama Zama tayi sukaci gaba da hirar jefi jefi har aka Kira magariba suka shiga sallah. Tana addu'oin yaumiyya na cikin du'aul mustajaba ne kira ya shigo wayarta da sauri ta dauko tana duba Mai Kiran Ummee ta gani da sauri ta daga tana fadin "Ummeena" Amsawa tayi suka gaisa Ummeen ke fadar an fada Mata ta kirane nan tayi Mata fadan rufe layi da tayi,nan Zahra taji kuka yazo Mata, Nan da Nan Ummeen ta rude tana tambayar ta ko tana da damuwa ne ta fada Mata cikin kukan tace "Ummee Shima fa wannan daga kawo ni gidansa ko sati daya ban rufa ba ya tafi ya barni Wai aiki zejeyi uk" shiru Ummee tayi kafin ta shiga rarrashinta da kalamai na kwantar da hankali da nuna Mata ba lallai ne hasashenta ya kasance gaskiya ba, kada ta damu saboda ita har Umara tayi bayan auren tayi mata addu'oin samun nasara akan dukkan lamuranta, sannan ta yi mata fadan ta kiyayi yawan kukan Nan bashi da ma"ana, daga karshe tayi Mata albishir zawan su next week harda Mama Hanifa da Aunty Nawwara duk suna hanya Daman ko Bata sameta a waya ba zata kira Hajiya Asma'u tasa a fada Mata. Murna ta shigayi Kamar tayi me har Ummee na Mata dariya Nan da Nan ta ware ta shiga lissafo abinda takeso Wanda za"a taho Mata dashi. Bayan maga wayarsu da Ummeen Ammah ta Kara kira lokacin tana tare da Abba. Tana zubawa Abba Dan fruit salad wayar ta dauki ringing Abban ne ya dauko ya duba 'yar dariya yayi Yana mikawa Ammar wayar tare da fadin. "Uwata ce ke kira". Ganin Kiran ze yanke yasa Abban karbar fruit salad din yaci gaba da zubawa Yana fadin "A dauki Kiran uwata kada ya yanke". Daukar tayi tana amsa sallamarta da gaisuwar da take mata. "Ammah yanzu Dan Allah bazakizo ba Kuma Aunty Hasana ma fa batazo ba fa Kuma Ni sonake na ganki". "Ikon Allah yanzu ke saboda Allah sai a ganni a gidanki a irin wannan kwanakin ai sai a dauka ba lafiya Auntyn taku dai zatazo Daman jiya take fad'a zata shigo ta ganki tunda mijin naki baya Nan, ai Mahmud din ma ya turowa Abban ku da sako ba dadewa ta whatapp yace sun sauka lafiya, ke dai abinda nakeso ki kwantar da kiyi Masa biyyayya kinji". Ta fad'a tana rarrashinta. "To Ammah, daman kira nayi na fada Miki Ummee tace next week zasu shigo Nigeria nasan zata fada Miki". "To Allah ya kaimu Daman munyi maganar shekaran jiya har take tambayar meya faru da taki wayar? Nace ta Dan samu matsala ne, ga Abbanku yace a gaishe ki" "Lah! Ammah Daman yana Nan amma ba'a fada min ba Bashi na gaishe shi" Sun gaisa da Abban har Yana Dan tsokanar ta, tunda a wani bangaren kakace a gurinsa, Nan yake fada Mata mijinta yace ya tafi da motarta Kano tana airport Dan haka daga nan Zuwa jibi za'a kawo Mata daya motar ta gurin Muttaka, godiya ta yiwa Abban sannan sukayi sallama. Ta jima Bata aje wayar ba, tana juya maganarsu da Ammah Wai ya fadawa Abba sun sauka wato ita da bayaso Bata da matsayin da ze kirata ko sako ya fada Mata sun sauka, kenan Daman duk abinda yake Mata a 'yan kwanakin Nan yaudara ce Dan ya lasa Mata Zuma a baki ya gudu ya barta da kewarsa inda ta godewa Allah be lalata mata rayuwa ta gudu ya barta ba wlh duk rintsi sai ta bar Kasar Nan ta koma Jordan, Dan tasan Allah kadai yasan halin da Ammah zata shiga idan bawan Allahn Nan yaqi dawowa.... ✨✨✨ ✨✨✨ AUREN HUCE HAUSHI. ✨✨✨ ✨✨✨ Story & Written by Naman Fateemah. page 31 ______________Har aka Fara Kiran sallar insha'i tana zaune tana faman tunanin makomarta, tashi tayi tayi sallah, nan Kan sallayar ta kwanta tana lazimi a haka har barci yayi awon gaba da ita. Tun zilai na saka ran fitowa Zahra har ta hakura ta shige ciki duk da ba barci take ji ba, tun yamma take ganin zahrar wani sukuku Kamar marar lfy. Zahra ba ita ta farka ba sai Kusan daya da kwata, tashi tayi tana mik'a tare da salatin Annabi, duk jikinta ciwo yake Mata hijabin ta cire tare da after dress din ya Zama daga ita sai vest da wandon toilet ta shiga Bata Dade ba ta fito canja kayan jikinta tayi da rigar barci ta Kashe wutar Mai haske ta kunna bed side camp tayi shiru tana istigifari ga Allah s.w.a da Salati ga fiyayyan halitta Annabin Rahama duk yanda tunani yaso ya bijiro Mata saida ta kawar dashi kawai ta fawwalawa Allah lamarinta tasan duk rintsi Yana tare da ita, a haka har barci yaci karfinta. Da safe har zulai ta Gama share share da mofin Zahra bata fito ba ganin shirun tayi yawa yasa tayi tunanin buga Mata kofa kada ta Zama babbar banza zuwanta ya Zama marar amfani rabonta da yarinyar nan tun magaribar jiya Bata Kara sakata a idonta ba, kofar bedroom din ta nufa tayi knocking taji shiru lokacin Zahra na Wanka, Kara bugawa tayi still dai shiru taji Nan da Nan hankalinta ya tashi kada fa wani abu ya Sami yarinyar Nan ta shiga uku. Tana Nan tana shawarwarin ta bude ta gani ko lafiya? taji alamun motsin tafiya daga ciki da sauri ta Kara knocking din, Zahra da towel a jikinta ta nufo kofar ta bude. "A'a Aunty zilai kece? Ina kwana?" Ta fada tana goge gashinta daya jike gurin wanka. "Lafiya kalau, naji ki shiru ne tun daga shiga sallah jiya harna gaji da zama Baki fito ba, gashi yanzu ma naji shiru har Ina kokarin Kiran Ammah na sani koba lfy ba". Ta fada tana kokarin barin gurin "na gode da kulawar ki Aunty zilai wlh jiya barci ne ya daukeni a nan Kan sallaya bani na farka ba sai Kusan karfe biyu na dare". "Ikon Allah kice kwanan kasa kikayi da sanyin tayis Bai Kama ki ba, tunda Naga gidan naku ko Ina sanyi Kamar gidajen larabawa". Sai Kuma ta rufe bakinta da hannu. "Kin jini ba wlh na manta Ashe gidan nasu ne". Dariya Zahra tayi "Kayya Ina wani balarabiya anan ai da uba ake ado Ni bafulatana ce kalarce dai na dauko tasu Amma idan masu abun suna yarawa wani abun sai kallo Dan ma Allah ya hadani da jarimin uba da yayi tsayin daka gurin ganin na iya yaren saboda na samu saukin mu'amala da dangin Mamana". "Wannan gaskiya ne Allah ya sakawa Alhaji da Alkhairi ya biya Masa bukatunsa na Alkhairi" "Allahumma Amin". Zahra ta fada. "Me za'a dafa miki? Mu dai nayi Mana nida bakon ku". "Wai bakon mu wato dai bazaki ce Mai gadin ba ko?. Dariya tayi. "Wlh baya Kama da masu gadi Kinga kuwa ai bana ce Masa ba". "Haka ne ki dafa min indo mie da cooker oat kawai". "To an gama sai kin fito". Ta fada tana juyawa zuwa main parlour din yayin da Zahra ta koma ciki. ************* DAMAGARAM NIGER REPUBLIC. Cikin takun ta na nutsatstsiya kuma wayayyar mace 'yar gayu ajin karshe ta shigo parlourn tana sanye da doguwar rigar madam gezber kalar peach sai gyalen kalar light yellow touching din flowers din dake jikin kayan sai takalmi plat Mai azabar kyau shima light yellow din tun kafin ta karaso kamshinta ya hade gurin. A hankali ya dago ya dubeta har ta karaso gurinsa, tattara aikin da yake yayi ya Maida hankali a kanta lokacin da take Zama a kujerar dake gefen da yake. "Sannu da aiki Yaya barka da Asuba". Ta fada tana sadda kanta kasa Bai amsa ba Jin shirun yayi yawa yasa ta dago kanta ta dube shi, ita yake kallo. "Yanzu abinda Kika zaba kenan Zainab da girmanki da hankalinki ki zazzage jiki ki baro dakin mijinki kizo ki nemi guri ki zauna mijinki yayi rarrashin duniyar Nan kinqi ki saurare shi daga karshen ma Kika zabi ki dawo Nan Damagaram saboda a Yamai uncle Yousoufu ya nuna Miki rashin kyautatawar abinda kikayi shine kikayo yajin Nan ko?.Ni tunda tubus ne Bari kizo ki zauna ki Mike kafa gashi nan har an Fara kawo Miki caffar ana son aurenki idan kin Gama idda wannan arzikin ki ne?". Ya fada Yana kureta da ido, da sauri ta cira Kai ta dube shi. "Ni Kuma Yaya ake jawo min zawarci kawai daga ganin mace sai ace zawara ce". "Kada kiga laifinsu sun ganki yau sun ganki gobe Baki da niyyar tafiya,idan Badi'a zata fita ki wanke jiki ku kama tafiya ba dole ace Miki haka ba". Idonta taf da hawaye ta dube shi "to Yaya ya akeso nayi kasan dai yanda abun Nan ya kasance duk yanda naso a saurareni idanuwa suka rufe ba Wanda ya kula da abinda nakeso su gane Saida suka rabani da Dana yabar gida cikin bacin Rai Wanda har gobe ba Wanda yasan inda yake, gaskiya Kuma tayi halinta yanzu za'a matsamin da zarya na fada musu niba yaji nayi ba duk ranar da yarona ya dawo Zan dawo". "Zainab a gabana kike fadar danki, Dan farin ba zakiyi min Kara ba". "Kayi hakuri Yaya na Bari d'anka to" ta fada. 'yar dariya yayi na nawa Kuma sai dai a koki gaba, yanzu Dan Allah Alfarma zakiyi min kiyi hakuri ki koma dakinki Suma sauran yaran suna bukatarki kusa dasu ko badan Babansu ba ki duba girman Hajiya Inna har Yamai Saida tasa aka kaita ko a jirgine dai ai tanayi dake ne amma Kika kasheta da dadin Baki akan kina tafe kikayi zaman ki karshe ma kikayo hijira daga can, duk laifin Hajja ne wlh ita an taba Mata dan 'yar so ba zaman lfy, gobe nace aje Abuja a daukeki tunda ba jirgin sokoto direct, kije kiyi ta yi masa addu'a bakin uwa Mai Albarka ne akan 'ya'yan ta muma muna tayaki nasan fushi yayi idan ya huce ze nemi gida". Har ranta bataso wannan hukuncin ba Amma yata iya da Yaya ishaq uba ne sak tun bayan rasuwar mahaifinsu bai barsu da kukan maraici ba, duk rintsi baya Bari su koka uwa uba yanda ya janyo gudan jininta ya nuna Masa hanyar nema tun a kananun shekaru duk abinda yaronta ya zama shine sila gashi Zuwa yanzu Allah yayi Masa karfin daya fi na Yayan. Hira sukaci gaba har Aunty Badi'a ta fito itama kamar me Zuwa gasar sarauniyar kyau ita Fara ce tas buzuwa kallonta Yaya ishaq din yayi "wato ta wata fuskar naji dadin zuwanki Zainab ko banza mutuniyar ta koyi gayu irin naki da dai sai a hankali". "Kai Yaya wlh bani na koya Mata gayu ba Daman Aunty na me class ce ko Aunty?". "Fada Masa dai,kawai nasan dai na koyi amfani da perfumes designers dani kowa ne ma saye nake Amma yanzu tunda ta bani naji dadinsu nake amfani dasu". Dariya yayin Yana fadin . "Ba cinya ba Wai 'yan magana sukace kafar baya, Wai yanzu Ina da kikace min zakuje? Bana son yawo har an Fara min sallama idan ta Gama idda". Ido Aunty Badi'a ta kwalalo "sallama Kuma?. "Wlh kuwa shi yasa nace ta tattara tayi hakuri zanyi Mata booking ta tafi kawai muci gaba da addu'ar Allah ya bayyana shi duk inda yake". "Gaskiya kam shi yasa kenan ranar da mukaje gidan sarki kingmakers sun fito daga meeting da Mai martaba Naga ana nuna ta har wani dogari Yana kokarin Zuwa gurin mu muka tafi". "Kinsan kuwa sakon daga fada yake". Baki Ammi ta rike "tab gara nasan inda dare yayi min kafin wannan labarin ya Isa kunnen general". Ta fada suna nufar kofar fita daga falon. "Da dai kin yiwa kanki gata" Yaya Ishaq ya fada. ********* Tun safe su Mahmud suka fita da Sameer su shiga can su fita can duk da Sameer Kusan Dan kallo ne an Kai ruwa Rana kafin a samu ganawa da Wanda alhakin matsalar ke hannunsa Basu suka dawo ba sai dare a gajiye suka dawo Jin dadinsu daya ba a hotel suka sauka ba gida ne. Sameer yayii musu order din abincin Africa. Saida sukayi wanka sannan sukaci abincin inda Allah ya taimaka sunyi sallah a wani masallaci a hanya. Bayan Mahmud ya shiga daki wayarsa ya Ciro ya shiga ciki gurin da akayi Masa connecting da CCTV nan ya lalace gurin kallon Zahra yanda yake more kallonta yasan da ace tasan da CCTV a dakin bazata Bata sakewa haka ba tana sabgoginta. Amma ganin ita kadai a dakin take zuba yanda takeso, amma yanda ya fuskanceta kamar wani Abu Yana damunta ya Raina yanda take walwalarta, ya rasa aikin me suke ita da Mai Taya ta zama Dan gani yayi ita Mai tayata zaman ta fita waje da alama wani Abu ta sawo Dan can baya yaga ta hada wuta da gawayi akan wani Abu ta Dora tukunya Mai Dan girma, so yake yaga wace wainar zasu toya. Dayar wayar ya dauko Yana kokarin kiranta sai kuma Kiran Mr Lee ya shigo akan Yana fada Masa kome yake ya fito bakin da zasuzo daga Thailand sun karaso shi kadai ake jira, tashi yayi Yana Kiran Sameer akan ya zama ready zasu fita. ** ZAHRA. Tun bayan data gama break Basu zauna ba aiki Zahra ta dauko dambun Nama take son yi yau akwai Naman da yawa sai kuma abinci shima Mai Dan yawa haka Nan taji tana son kaiwa Abban ta da Baba Malam abincin juma'a zilai ce tace a sawo kufat ayi suyar dambun a Kai tunda da yawa za'ayi ta Bata kudin aka sawo ta Dora, Basu suka Gama aikn ba sai bayan azzahar zilai ita ta mikawa zayyan bayan ta wuce ne ya bude abincin yaga irin garar da aka kawo Masa yayi ta mamakin yanda matar oga ta iya girkin hausa haka Mai shegen Dadi gashi ita Kuma ba bahaushiya bace ko Ina ya samo wannan da Kuma dalilinsa na zabar wannan rayuwar shifa ko a mafarki baiyi tunanin ogan nasa ze iya sakewa har ya Mike kafa yayi zamansa a irin wannan muhallin ba da iyalinsa, haka yayi ta sakawa Yana kwancewa. Sai da su Zahra suka Gama Zuba komai a mazuban da suka Dace sannan Zahra ta wuce ta Kira magaji a waya akan yazo tana nemansa sannan ta shige wanka sai bayan la'asar magajin yazo lokacin ita kadaice a falon tana tulawar alqur'ani, Saida ya cika cikinsa Yana zuba Santi sannan ta bashi yace ta fito Masa na Baba Malam Dana gurinsu Ammah har ya Kai kofar fita daga parlour ya juyo Yana fadin "inyeeh su Adda Zahra an girma har an Fara aikin neman ladar tsaffi da fatan dai kin fadawa mijin naki kada garin neman lada a kwaso zunubi". Ya karasa fada Yana dariya. "Allah ya shiryeka magaji Kai Kullum baka girma ko?" "A'a zancen gaskiya ne Dan bawan Allahn nan baki San yanda yayi ya Nemo kudin sayen kayan nan ba Amma kin tashi kin zuba irin wannan garar Dan kawai Kinga baya gari ko?" Harararsa tayi "To nayi kayan nan dai nawa ne mijina ya aje min Bai Kuma yi min iyaka ba duk abinda nakeso zanyi dasu idan bazaka Kai ba dawo ka aje min sai Aunty zilai ta Kai ko naje da kaina". Ta taso ta nufo inda yake da sauri yayi gaba Yana fadin. "Allah ya huci zuciyar uwar gidan Mahmud tuba nake". "Dan rainin hankali shi dai gurinsa ya saka mutane magana". Aunty zilai ce ta Bata amsa Sam Bata lura da fitowarta ba. "Kema uwar dakina Kamar kin manta halin Mai sunan Alhaji ai shi burinsa Ke nan yayi jan magana". "Ai sai yayi tayi tunda halinsa ne" Abincin zilai ta kawowa Zahra Nan cikin parlour some times Bata fiye son zaman dining ba, kitchen zilai tayi niyyar komawa Zahra ta Hana "ki zauna a nan muyi lunch din Ina Zaki kuma koni bafulatana bana irin wannan d'abi'ar". Sun Fara cin abincin kenan door bell din tayi k'ara zilai ce ta tashi taje ta bude Mujiba ce tare da wata yarinya Sa'ada 'yar makotansu. "Kai! Kai!! Kai!!! Tab amma dai batan hanya kikayi Mujiba, yanzu Alkawari da amana sunce haka? Yaushe rabonki da gidan Nan?" Dariya mujibar tayi tana fadar "eh lallai da sauranki irin wannan Baki zai- zai, Kuma shike Nan daga kawoki saina dunga sunturi a gidanki ai Mai gidan saiya saka Mai gadi ya hanani shigowa tinda Zan zamar masa matsala, Wai ke tsaya waye a gate din gidan nan daya tsaremu da dogon turancin daga Ina zuwa Ina me mukazoyi ke tambayoyi dai gasu nan kamar zanga Mrs president". Ta fada Tana Zama a kujerar dake kusa da zahrar Sa'ada ma ta zauna. Spoon din hannunta Zahra ta aje "Bari kawai Muji wlh Nima haka na ganshi haka Nan Rana tsaka ya canzawa Mai gadin gurin aiki ya mayar dashi makarantar gidan Baba Malam ya ringa share share ya kirawo wannan bansan ko daga Ina ba yanda aka wayi gari da Mahmud shima haka aka ganshi nifa lamarin yafi karfin tunani na kawai na saka ido ne Naga karshen film din". Ta fada tana Dan tab'e Baki. "Amman wlh Baki da kirki auren naki kike cewa film dan bawan Allah ya biya sadaki ya daukoki daga gidan ku ya killace ki guri daya ya Baki ci da Sha amma ki Kira Masa aure Shirin film humm zakiyi bayanin film da alama komai normal yake tafiyar Miki ko Aunty zilai?" Dariya tayi "A'a babu ni a cikin wannan maganar kunga tafiya ta". Ta wuce kitchen da plate din abincin ta. " Kinga Sauko kiyi serving din ku, ni ban iya abinda Kika iya ba ku Kenan bakinku ba kintsi ku dunga sakin magana irin haka Ina Dadi Kinga kin Kori Aunty zilai daga wurin". Tasowa tayi ta sauko kusa da zahrar tana fadin "lallai kina Jin Dadi irin wannan garar haka sauko sa'ada Wai Ina Mai gidan na Dan kwana biyu ban ganshi ba?" Plate din ta ture gefe ta dauko tissue tana goge bakinta. "Yayi tafiya jiya baya Nan". Tsayawa mujiba tayi da cin abincin. "Bayanan Kamar ya?" "Kamar yanda na fad'a Miki yaje taron gamayyar Qungiyoyin da suke taimakawa ilimin makarantun government Dana allo a Nigeria da wasu kasashen Africa, to a Nan zone din namu na north east shine aka dauka a Bauchi state, a jigawa da Kano ma duk suna da nasu wakilan tunda state uku suka dauka". "Masha Allah kice wata Rana ku sai turai tunda Mai gida ya Fara irin wannan babbar harka ai ku hannu sama chololo lallai mutuniyar kinzo da goshi". Tsaki tayi wlh ki raba kanki da camfi Wai nazo da goshi to tun kafin nazo yake aikinsa Kuma tafiyar ma dagawa sukayi tun ba labarina a rayuwarsa zasuyi abarsu Nima da abinsa na same shi sai yanzu ne dai ta Kara tasowa. Haka suka dunga Hira har Kusan magariba sannan suka tafi Zahra ta Basu kilishi da biscuits masu yawa. Saida magaji ya Fara Kai sakon Baba Malam sannan ya karasa gida, yauma aikin Ammah ne lokacin daya shiga parlourn ta ba kowa sai Alawiyya tana saka turaren wuta da freshner tambayarta yayi Ina Ammah? Tace Masa taji dakin Abbansu can ya nufa da basket din da ledar knocking tare da sallama a kofar falon Mamace ta amsa Masa ya bude ya shiga da alama wani Abu suke tattaunawa. Gaishe da Abban yayi sannan ya gaishe dasu Ammah Yana aje basket din da ledar Naman da aka kunshe cikin poil paper. "Abba gashi inji Adda Zahra tace a kawo maka". Mama ce ta taso tana fadin"Kai Masha Allah lallai wannan 'yar tana ji da Abbanta". warmers din ta Fara cirowa tana bude miyar falon ya cika da kamshi Curry da spices. "Abban ne yace "magaji sannunka Kaima lallai uwata ta haifu Allah ya yiwa wanna aure Albarka ya tsane idon makiya wlh naji Dadi kwarai da gaske a Miko min nan Naga abinda uwata ta kawo min". Ya fada Yana mik'awa magaji bugun Abuja biyar zuwet. "Na gode Abba, Kuma ta bada an kaiwa Baba Malam ma ya fada Yana nufar kofa. "Masha Allah nasan uwata zatayi abinda yafi haka". Cikin rawar jiki mama ta kinkimi basket din ta Kai gurin da Abban yake zaune ta dora akan coffee table, sannan ta dauko ledar, ledar yace ta bude lafiyyayan dambun naman rago ne yasha kayan Hadi ya sayu jawur dashi sai Kamshi ke tashi, Dina yayi yakai Bakinsa ya tauna Yana fadin "Masha Allah uwata ta Gama min komai wlh har Raina Ina son yarinyar Nan bilhaqqi uba ta daukeni sak duba ki gani Rabi'a ga Asma'u a zaune amma Ni ta yowa wannan garar Kai madallah, Yau abincin ki sai dai yayi hakuri na uwata zanci". Ya fada yana kallon Ammah. 'yar dariya tayi Ammah tana fadin "Ana ta sabon d'a wa yake ta tsohon da inji barmani choge". "Gaskiya kam, ai Babu Mai shafewa Zahra Zane a gurin Abba" Mama ta fada. "Ki Fadi ki Kara Zahra yarinya ce mai tsananin yi min biyayya ki duba yanda lamarin auren Nan ya kasance Amma tunda tayi 'yan koke-kokenta ta hakura ba Wanda ya Kara Jin kanta, duk da mijin nata Mai Karamin karfi ne akan wadanda suka nemi aurenta Allah be nufa ba da Kuna duba da inda ta fito da Kuma uwa uba dangin mahaifiyar ta Amma tayi zaman ta Ni kuwa ba abinda bazan yi Mata ba matukar baifi karfin arzikina ba". "Wannan gaskiya ne duba da yanda ta waye tayi karatu Mai zurfi ai ba wata ce bijirewa zatayi ayi ta Kai ruwa Rana" Mama ta fada. Yar dariya kawai Ammah tayi duk Dadi ya cikata Bata taba tunanin Zahra nada wayo haka ba tasan dai abun duniya Bai rufe Mata ido ba. ✨✨✨ ✨✨✨ AUREN HUCE HAUSHI ✨✨✨ ✨✨✨ Maman Fateemah. Page 32 _______Qaran alarm din daya saita ne ya tashe Shi sallar Asuba, duk da bai kwanta da wuri ba Dan sai Kusan karfe biyu na dare suka shigo gidan, meeting din nasu sun jima suna tattaunawa akan sabon kafanin da zasu bude a jihar kebbi na shinkafa, masallacin da suke sallah da gidansu akwai tazara sosai shiyasa ya saita kafin sallar Asuba da kamar hour daya, sai da yayi yaqi da Shaidan sannan ya samu ya sauko daga gado Bai jima a toilet ba ya fito sanye da bathrobe Fara tas Mai jikin towel. Jallabiya ya saka yayi raka'atanul fajri sannan yayi waje a Yana niyyar yiwa Sameer knocking ya bude ya fito. "Barka da Asuba" Sameer ya fada yana mikiwa Mahmud hannu sukayi musabaha, "Ashe ka tashi ai nayi tunanin saina shafa maka ruwa sannan ka mitsa". 'yar dariya Sameer yayi Yana fadin "irinku da kuka San inda kuka dosa Kuna dagewa da mujahada to mu ta Yaya zamuyi kwance muna barcin asara ai sai lalacewa tayi yawan". "Kayya Kai dai Allah ya datar damu kawai" "Allahumma Amin" Sameer ya fada lokacin da suka jero suna Kara tattaunawa akan harkokin yau da Kullum, Sameer ne yaja musu motar suka fice daga gidan, bayan sunyi sallar zama sukayi akayi karatu Kusan masallacin mahadar 'yan Africa ne mazauna can Kusan duk Wanda yake a kukkuken gurin Baya Bari khamsu salawat ta wuce shi, sai da gari ya waye sannan suka nufo gida. A hanyar ne Sameer ke fadawa Mahmud sunyi waya da Habib jiya a kan training din da za'ayi na matasa maza da Mata na koyon sana'a. Har suka zo gida suna zancen, yaso yayi barci amma ya fasa, so yake ya Kira Nigeria baze iya mazewa ba Kamar yanda yayi niyya Bai gane shi Mai rauni bane sai akan yarinyar nan,sai da yayi Mata nisa ya gane shayi ruwa ne, duk da Bata shigo rayuwarsa da Wasa ba kafin ya hadu da ita shi jarimi ne sannan shi baima fa San yanda kake kwana da Abu ka Kuma tashi dashi, shifa idan ya tunata har wani ji yake zuciyarsa ta harba, yaso ya dan Bata iska, so yake ya fahimci shin ta karbeshi da zuciyarta da gangar jikinta ko Kuma har yanzu tana zaune dashi ne by force na iyayenta, amma idan ya kalli kwayar idanunta Yana hango wani Abu na daban a cikinsu Kuma uwa uba yanda sukayi rayuwa a Dan zaman da sukayi da ita. Bayan sun shiga gida kowa nasa gurin ya dosa Dan shi dai Sameer barcin ya kama, shi kuma daya shiga wanka ya sake, shifa idan ze wuni Yana zubawa jiki ruwa bashi da damuwa. Sai da ya gama komai ya Haye gado daga shi sai singilet Fara sol da boxer short. Wayar ya dauko dauko cikin ikon Allah yaga Zahra online ji yayi wani Dadi yaji ya rufe shi, vedio call ya Kira daya wayar Kuma ya bude connection din CCTV. Tana cikin charting da Aunty Nawwara kawai kiran nasa ya shigo Yana kallon yanda ta kwalalo Ido waje abin har yaso bashi dariya, hijabin da tayi sallah ta dauko ta rufa kirjinta sannan ta daga Kiran suna hada Ido taji gabanta ya Fadi ji tayi abun Nan na da ya dawo Mata. Sallama yayi mata da husky voice dinsa wanda ya saukar Mata da wata muguwar kasala, a hankali ta daga idonta ta kalleshi cikin murya Mai rauni da rashin karsashi ya amsa Masa sallamar, kuri yayi da idon Yana kallonta yanda tayi Masa wani irin kyau Kamar shi gani yayi a tsakanin jiya da shekaranjiya Kamar an Kara Mata kyau. "Ki bude Ido ki kalleni ki bani labarin abinda ya faru daga tafiya ta Zuwa yau, kuma wlh ki cire hijabin nan tunda ba sirikinki bane Ni da Zaki dauko hijabi ki Kama rufe jiki wato Ni ban cancanta Naga abinda yake halalina ba ko?" Kai ta girgiza tana masa kallonsa a shagwabe. "Nifa tunda nayi sallah nake sanye da abuna bawai saboda Kai na saka ba nida bansan zaka tuna Dani bama ballentana ka kirani, nifa na dauka Kama shafe babina tunda baka nemana wanda ka damu dasu kake nema". Ta fada tana juya sexy eyes dinta wanda Bai sani ba ze dauka da niyya tayi Hakan. Ajiyar zuciya yayi Yana Hadiyar yawu shifa ganin Nan da yayi Mata ta jangwalo masa wata fitinar da sai Allah kawai. "Ki cire hijabin Nan Allah kona Baki mamaki". Kafada ta make tana kallon gefe Dan wani fitinan nan kallo yake Mata. "Dan Allah ka dena kallona". "Ikon Allah wato naje nayi ta kallon Mata a titi kenan ba ruwanki ke ko irin 'yar kissar Nan ta Mata Ni baza'ayi min ba tunda ni ba Mai aji bane banyi boko mai zurfi ba ko "Ni kuma? Yaushe nace bakayi karatu Mai zufi ba?" Yar dariya yayi irin ta kana cikin ?nishadi din nan. "Wato wayo zakiyi min na bar maganar hijab wlh ki cire Kona biyo dare nazo Nigeria na.... "Dan Allah ka Bari wlh Zan cire kada ka fada". "Ki Bari kiji mezance Mana my previous". Ya fada Yana Kashe Mata ido. Itafa mamaki yake Bata idan Yana fadar wasu kalmomin turanci sai taji Kamar zurfin iliminsa ya wuce yanda ake fada, ta ko Ina a waye yake ga wata irin tsabta ta ban mamaki itafa idan ba karya idonta yayi Mata ba sai tace Bata taba ganin ya Mai maimaita Kaya ba idan ya saka Bata qara ganinsu a jikinsa. "Wlh kiyi abinda nace kona baro Miki aikin da Baki shirya Masa ba, 'yar yarinya dake kin hana zuciyarta sakat tunda na Dora idona a kanki komai ya kwance min duk, akanki na iya tsayawa nayi doguwar magana na iya ja in ja akan Abu duk soyayata da Hajiya Innata saida mukahau sama da ita mukayi uwar watsi nayi Mata yaji Kuma haka kawai Allah ya dubi diminiya ta ya tausayawa Dan malam kiyi min rowar ganin halalina, wlh Zan fadawa oga Sameer ayi min afuwa na dawo gida na fasa attending din meeting din a saka wani na dawo na rungumi 'yan kayana". " Wai Kai baka jin komai idan ka Fadi magana! Dan girman Allah kayi zamanka kayi abinda ya kawoka in dan hijab bari ba cire. Amma Dan Allah ka Bari na saka riga Allah ba kaya a jikina sai vest". Wani kallo ya jefeta dashi na Amma kin Raina ni. "Dan Allah, wlh kunyarka nakeji da gaske" Ta fada tana sunkuyar da Kai kasa. "Kunyata ni Kuma wlh immediately kuwa Zan cire kunyar Nan aini cutuwa zanyi, To wai tsaya na tambaye ki yaushe Hakan ta faru? Ko bayan na baro kasar ne ki? amman ai bakya jin kunyar kallon tsabar idona ki tarewa wani Kato fada Dan nace masa lusari kika Kare min tas har kina fadin na Kama ki na runguma ko kina min kallon Dan duniya ko? humm Ashe ma duka nine lucky din a cikinsu dama na San abin nawa ne Aida saina dama daddawata da moda a lokacin Dan wlh a Ranar sai da na Raina kaina Banda mutum besan gobensa ba Aida saina Yi wandaqata a lokacin" fuskarta ta rufe da tafin hannunta dayan, da gaske so yake ya koya Mata fitsara taga alama shima ba kyalle bane cikakken zani ne. Idonsa ne ya sauka q gurin data cire hijabin. "wow!! Masha Allah! Koke fa Amma da kin zumbuda hijabi Kamar wata matar liman ai yanzu hirar zatafi Dadin yi ki kawar min da tunani kowa daga zuciyata sai naki, Baki fada min abinda kukayi jiya ba Naga harda spare girki a waje" . Zaro ido tayi tana dubansa "waye fada maka nunyi wani Abu a gudan? "Nina gani kinsan nabar idona daya a Nan na taho da daya, ga Kuma Dan gidana magaji shine yayi min voice note ya bani labarin selfishness din da kikayi na kawai su Abba Kika garar arziki ta juma'a Kika ware min iyayena Mata, shi yasa Kika saye zuciyar su Abba da Baba malam kenan,? Kullum maganar daya ce ga amanar yarinyar Nan ka kula da ita Ashe dai tushiyar Baki kike bayarwa". "Kai wlh ba haka bane ai gani nayi idan na kaiwa Abba Kamar na bawa Ammah ne, haka Baba malam ma ai Iya Abula na bawa koba haka ba" "Eh kusan Hakan ne amman dai da gyara, Kuma kike wani cewa Abula ko 'yar Karar Nan Babu nifa sunan tsohuwata ne,amma kici gaba da fada wata Rana kunya zakiji idan Kika fada a gabanta tunda bakinki ya Saba fada kinsan dai mu mutanen karkara bama Raina abun fada can zakiji zance ya zagaye cikin kauyen mu ace Mamuda ya auro 'yar birni ko sunan Inna Bata sayawa gatsau take fada". Kai ta Dade tana tadan turo Baki irin na sakatattun yaran Nan tana fadin "Nifa ban sani ba Ina janta ne tunda sunan kakata ne babar su Ammah zakace min waye waye nima ai Mamana ce ba taka bace Kai kadai yanda kayi kutse a gurin Amma Nima haka zanyi a gurin Mamana harda Hjy Inna". "Kice nayi celebration ana son da Ammi, inye matar Mahmudun ba, fada min wace addu'ar kike min Dana kasa kallon ko wace mace da sunan so tun bayan kin shigo rayuwata, da dai bana musu da kowa Amma a kanki humm har bore Saida na koya, oya fada min sirrin inji?" Shiru tayi saboda ji tajeyi kamar zir take a gabansa, Amma ta lura shi ko a jikinsa kamar ma be damu da yanda take din ba. "Kinyi shiru ko abun sirri ne baza"a fada min ba?" "To me kake so na fada maka". "Komai ma, me kike fadawa samarin ki idan sunzo zance? Nima yau zancen nazo Wanda ban samu damar yi ba a baya shine yanzu nike qara'i". Batasan sanda tayi dariya ba "Au dariya ma na baki ko? Shike nan wlh nifa a kanki na iya zance me yawa da mace ada daga Ammi sai Hjy Inna kawai nake doguwar Hira sadu, nasan duk ranar da Hjy ta ta ganki sai tayi Miki ciwon Baki tace dan kwali yaja hula kinsan meta fada lokacin Dana fada Mata mgnr ki?" Girgiza kai tayi alamar A'a. "Cewa tayi idan na cika cikakken namiji na shiga duniya na nemoki, Ni kuma nayi wani Alkawari daga ni sai Allah saina bata mamaki wlh". Kama Baki tayi tana Dan Zuba masa sexy eyes dinta wadan da ke rikita Masa lissafi. "Kakar taka zaka bawa mamakin duk soyayyar da kake yi Mata kace za'a ganku a rana?". Kai ya gyada Mata yana gyara kwanciyarsa. "Yes ai kece mahadin aikin da zanyi na Bata mamakin ko bazaki tayani ba?". "Ni kuma meya hadani da dabin ku?" "Kina son sani na fada Miki?" "Uhm". Karan doorbell ne ya dakatar dashi daga kokarin bayanin da ze Fara mata. "My precious Afuwan naji ana bukatar shigowa Bari naje I will call you later, take care by". Ya tura mata wani hot kiss Yana kashe Mata ido ya sauka daga online din. ******** DAMAGARAM. Waya ce a kunnenta tana magana cikin tsantsar ladabi kamar tana gaban Mai magabar, cikin ladabi ta Fara fadin "wlh Hajiya ba haka na fada Masa ba cewa nayi kada ya tura kowa Abuja nayi booking din flight ne daga Abuja Zuwa sokoto, tunda Yaya ishaq jirgin Abuja ya yi min booking Kuma nace masa ko nazo sokoto bana son a turo min kowa yanda na fita Ni kadai haka bake bukatar dawowa ni kadai kinji yanda mukayi dashi ai nace masa Zan dawo Amma gani yake kamar gaba zan karayi" "To ai yanda Kika gindaya Masa dokar ne yake tantamar hucewar taki, kiyi hakuri Zainab anyi Miki ba dai daiba Amma ki zama mai yafiya akan laifin da akayi Miki kema sai Allah ya yafe Miki naki kura kuran, ki Kara godewa Allah kece karama ke Kuma Allah ya daukaki naki Dan fiye da kowa a dangi ki dauka abinda ya faru jarabawarsa ce tazo a haka,Daman Allah swa yace shin bana jarabceku ba? to ki dauka hakan rubutaccen al'amarine daga Allah idan aka daure wata Rana sai labari, shi ba yaro karami bane da za'ace ya bata kawai yayi Mana fushi ne inaji a jikina Yana kusa da dawowa garemu da izinin Allah, ai kawunsa mustapha yace min ba abinda ya tsaya a harkokinsa Dan yana bibiyar lamuransa a yanar gizo yaga komai yana tafiya daidai". "Nima Ina bibiyar lamarin nasa Hajiya Amma abinda yafi damuna koni bai taba kirana ba ko sau da har zuwa Yau". "A'a Zainab mu duka masu laifine lokacin daya kamata a saurare shi kowa baya ya juya masa, Banda Mai biyaya bane yanda Allah ya daukaka shi ko ganinsa basai yayi Mana wahala ba? Amma yaro Mai ladabi da biyyayya mun taru mun yi masa naqi ba dole yayi nesa damu ba". Saita balle da kuka, da kyar Ammi ta lallasheta tayi shuru. Sannan tayi mata sallama tana Kara jaddada Mata zuwan tare da fadin ta turo direbanta ya daukota Dan gidanta zata sauka tunda anan tabar motar data zo gurin Hajiyar da ita a Ranar data wuce YAMAI. Aunty Badi'a ce ta karaso kusa da Ammin tana fadin "ina ganin soyayyar uwar miji da matar d'a amma ban taba ganin irin taku ba inaga yanda Hajiya Inna ke sonki ko Yallabai Bata so haka gashi ta kwallafa rai kan Mahmud kamar me" Zama sukayi a Kan sofa daya dake cikin dakin. "Wlh Ni kaina Aunty Ina jinjina yanda Hajiya ke Sona da dukanin yarana shi yasa sau da yawa idan wani Abu ya taso a gidan bana Bari taji ko labarin sa Dan nan da nan zata tashi hankalin gidan sai Kuma abun ya Zama wani Abu daban Dan Kullum gani sukeyi na Gama da kowa a gidan ballentana abinda ya biyo bayan rigingimun da akayi wanda suka saka na baro musu gidan,sai Abun ya Kara zafi ganin irin tujarar da general yayi da irin hukuncun daya yanke". Dan nisawa Aunty Badi'a tayi kafin tace. "Abinda dai baiyi tsabta ba Kam sai dai fatan Allah ya kiyaye gaba, Daman shigowa nayi muyi magana akan hukuncin da Zaku yanke ne hada Mahmud Aure da 'yar aminiyarki matar takawa, tun a jiyan naso mu tattauna sai nayi Baki sauka cinye lokacin, me ze Hana ki Bari aga dawowar tasa tukunna sannan kiyi masa tayin yazo yaga yarinyar idan Allah yasa tayi masa a irin matar da yake ra'ayin ta Zama iyalinsa Kinga shike Nan idan Kuma an samu sabainin haka Daman ba'a amsa ba bare zumuncin ku ya samu matsala ko ya Kika gani?". Shiru Ammi tayi tana nazarin maganar matar yayan nata Kuma 'yar uwa abokiyar shawara. "To ai abin dubawa Aunty kada fulani taga ban kyauta mata ba tayi min na huce ace na buda Mata kasa a ido bazan iya ba, idan Allah ya dawo dashi mijin mace hudu ne idan Yana da wadda yake muradin aure ya Kara da ita Dan nasan bazeki Haura'ul Insiyya ba, duk abinda ake nema ga Diya mace Allah yayi Mata ga uwa uba nasaba". "Haka ne Allah ya dawo Mana dashi lfy ya Kuma zaba abinda yafi Alkhairi, Amma dai in ina Raye wlh ba Mai yiwa yarona dole ba ruwana da Amincin ku can tsaninku" Baki Ammi ta Kama tana Fadin "Tofa kaji masu 'ya'ya wato kin nuna side ko?" "Ki fadin koma meye Amma dai a barmin yaro ya samu peace of mind gaskiya, shi bashi da idon ganin matan ne? Ina cewa kasashen duniya yake yawo Kinga kuwa wane irin Mata ne be gani ba, Kuma da bakinki kike fadin yace shi da wadda yake so daman biyayya ce kawai zeyi ya karbi auren da aka bashi Amma komai Daren dadewa zeyi wani auren to ki cire kanki a cikin jerin masu tilasta 'ya'yan su auri abinda sukeso, ki bishi da addu'ar Allah ya hada shi da abokiyar Zama ta gari kawai, se kimarki ta karu a idanunsa ki Zama abokiyar Shawarar sa babu abinda ze rufe Miki Amma kina shigo Masa da irin wannan zance ze Miki wani aji na daban, baze saki jiki dake ba balle kisan menene matsalarsa, ki tsaya kiyi nazarin abin nidai shawara ce na baki" Tunda Aunty Badi'a ta Fara Kora bayani jikin Ammi yayi sanyi saboda suk abinda Aunty Badi'ar ta fada gaskiya ne, nisawa Ammin tayi "haka ne Aunty wannan observation ne me kyau hakan zanyi Daman fulanince ta Fara kawo maganar Naga Kuma ya dace na Bata goyon baya, Amman in Sha Allah zanbi Shawarar ki...✨✨✨ AUREN HUCE HAUSHI ✨✨✨ Page 33. MAMAN FATEEMAH. ________Zahra ta Dade a kwance tana sakawa da kwancewa, wani irin yanayi takeji a jikinta ita abun har mamaki yake Bata "Wai menene hakan" tayi tambayar da ba Mai Bata amsa. abinda takeji wani Abu ne na daban Wanda Bata taba Jin irinsa ba akan kowane da namiji ba, cikin kankanin lokaci ya cika Mata zuciya ita abun har kunya yake Bata,ta gama bore harda su somewa dasu wunin Asibiti Kuma yanzu a wayi gari a ganta dumu dumu cikin soyayyarsa ai da kunya wlh. Wani tunanin ta qarayi Bata San lokacin data rufe idonta ba tana ambaton "Ya Ilahiy wlh abun da matukar Allah ka agajeni gaskiya idan hakan ta kasance naji kunya". Ta fada tana qara qanqame jikinta. Saida ta Kusan Bata minti talatin tana abu daya sannan ta yunqura da kyar ta tashi,wanka tayi ta shirya cikin English wears yellow irin shaking material din Nan sai sukayi Mata wani irin kyau Karamin mayafi ta rufe gashinta dashi black Mai shara shara ana kallon bakin gashinta Mai santsi da laushi ta cikin gyalen, sama sama ta fesa turarenta ta fito parlourn ba kowa sai kamshin freshner da turaren wuta kawai sai Kuma sanyin A/C daya ratsa ko Ina,cikin takunta na nutsuwa ta doshi kitchen inda take jiyo motsin zilai a cikinsa. Sansanyan kanshi ta ya Fara shiga hancinta zilan kafin ta karasa shigowa. "Masha Allah! Uwar dakina dawisu sarkin ado, Allah ya barki gidan Yallabai muhmudu, ubangji ya kawo Mana kazantar daki Amma Bata shara ba". Dan murmushi Zahra tayi tana Fadin kin jiki Aunty zilai ni kibar wannan maganar gaskiya, Ina kwana". Ta fada tana komawa parlour biyota zilan tayi tana Fadin "yau fa abinda kikafi so nayi Miki" ta fada tana kokarin bude warmers din abincin,waina ce manya irin tasu ta Bauchi sai Kuma pepper soup na cow leg da kunun gyada Wanda yaji Madara. "Wow! Amma aunty zilai kin gama min komai na gode" ta fada tana janyo plate din da zata Zuba, zilan ce ta karba da sauri tana fadin "haba dai gani a tsaye Zaki Zuba abinci da kanki to meye amfanina". Rike plate din Zahra tayi tana fadin "Dan Allah kada muyi haka dake Ina laifin dafawar ma ai dadin sai yayi min yawa, Ina kwance Ina barci kina ta faman dawainya sannan Zuba abincin ma Sai anyi mini". "To menene ai aikina ne". "A'a wlh ba Aikinki bane a Nan cewa akayi ki tayani Zama kwarai". Ta fada tana bude abinci akan dole zilan ta hakura ta koma kitchen inda take wanke waken alale zatayi musu cikin abincin Rana. Bayan ta Gama yin break din parlour ta dawo ta kunna tasharta mbc max tana kallon wani film da sukeyi, tana Nan zaune taji karar door bell ta tashi ta nufi kofar ta bude yara ne kamar 'yan sheka sha uku haka suna rike da manyan ledoji kowa guys biyu a hannunsa. Cikin girmamawa suka gaishe da Zahra tare da fadin "gashi inji Baba Malam yace a kawo Miki Kuma Yana gaishe ki". Suka fada a tare, hanya ta Basu suka shigo da kayan ciki sai raba Ido suke suna kalle-kalle. "Sannunku ku aje ku zauna, na gode kwarai da gaske Allah ya saka da Alkhairi, a me kukazo ne?". Dayan da yafi magana yace "Yaya Habibu ne ya kawo mu Yana kofa gurin wancen mutumin" ya fada Mata. "Masha Allah". Ta fada tana Kiran zilai, da sauri ta fito tana fadin. Gani uwar dakina". "Kaya ne Baba Malam ya Aiko aka kawo min". Gurin da kayan suke ta karasa tana fadin "Masha Allah 'yar gatan Baba malam, an gode madallah sai a Basu tukwaici". Zilan ta fada tana kokarin bude ledar dake kusa da it's. "To Bari na dauko musu ki shiga da kayan ciki sai ki zuba musu abinci a robobin nan na take away Wanda aka kawo saboda zuba kayan gara Dan kada su zauna yau Ranar wanki da 'yan aikace aikacensu ne," ta fada tana yin gaba. Bedroom dinta ta shiga ta duba Sam ba kudi a gurinta, Dan Jim tayi sai Kuma ta bude bedside locker ta dauko keys din dakin Mahmud daya Bata. Kamar' Mai tsoron wani Abu kada ya kamata ta bude dakin, komai tsab hatta kamshinsa Yana dakin kamar yanzu ya fesa yabar dakin,limshe ido tayi tana shakar kamshi, komai na dangin electronic a kashe yake a dakin a hankali ta ratsa ta nufi inda ya nuna Mata yace idan bukatar wani Abu ya tashi ta dauka, locker din ta janyo 'yan dari biyar ne da dubu dubu ko wanne rapper uku uku 5k kawai ta Ciro daga cikin 'yan 1k din ta mayar ta rufe tana tunanin Kiran magaji yazo ya Ciro Mata kudin saboda irin haka Bata bukatar komai tunda ba abinda ba'a aje Mata ba wani abun ma Sai a shekara Bata nema ba. Bayan ta kawo musu sukayi gdy suka fita, gurin Aunty zilan Zahra ta shige. *********** Karfe biyar na yamma jirginsu Ammi ya sauka a sokoto, lokacin data fito Harabar da masu jiran saukar 'yan uwansu suke,Habu direban Hajiya Inna ne ya nufo Ammi da sauri Yana fadar "barka da sauka Hajiya, nine Hajiya Inna ta turo nazo na tare ki". Ya fada Yana karbar karamar luggage din dake hannunta . "To sannu da kokari nagode kwarai". Direct gidan Hajiy innar ya nufa da ita da yake unguwar mabera, duk yanda Abban su Mahmud yaso ta zauna part dinta daya Gina Mata Amman ta nuna tafi son daga nesa dai. Har kofar falon Hajiya Malam Habun ya kawo ta bisa umarnin Hajiya, lokacin da ze tafi dauko ta fada masa ya kawo Mata ita har kofar parlour. Kafin ta fito Yara qananu guda biyu suka fito da gudu daga parlour wanda yayi dai dai da fitowar Ammi daga mota da gudu suka karaso, suna fadin ga Ammi! Ga Ammi" suka fada jikinta a tare suna fadin "Ina kikaje Ammi Baki tafi damu ba mukayi ta kuka". Kansu ta shafa tana fadin "sorry My babies ba gashi na dawo ba, ai kuka Kuma ya Kare" Hannunsu ta rike ta nufi kofar da suka fito, sun riketa ram kamar zata gara guduwa ta barsu. A zaune Ammi ta samu Hajiya inna tana lazumi, gurinta ta nufa cikin takunta na nutsuwa tana fadin "Hajiya barkanmu da yamma". . Ajiye tasbahar dake hannunta tayi tana kallon Ammi wadda tayi wani tas da ita, bazaka taba cewa ta aje kamar' Mahmud ba, idan aka jera su mafi yawan mutane zasu ce yayarsa ce. Gefen Hajiyar ta zauna daga kasa wannan d'abi'ar ta ce Bata taba Zama a kujera matukar Hajiya na Kan kujera, cikin ladabi irin na D'a da uwa Ammi ta gaishe da Hajiyar Tana fadin "Masha Allah zainabu kin cika Alkawarin da Kikayi min Koda kuwa ba a lokacin bane nagode kwarai da gaske Allah ya Albarkaci zuciyar ki ya Baki rinjaye akan duk masu son su tagayyara Miki zuri'a, ki Kara hakuri akan Wanda kike yi lallai duk Wanda akace yayi hakuri an Bata masa ne, Allah yayi Albarka yanda kike min biyayya kema Allah ya Baki surukar da zatayi Miki fiye da yanda like min, Wai kin samu yin magana da mutumina kuwa bayan munyi wayar nan?". "A'a har yanzu be nemi kowa ba ina ganin ko ba lafiya ba dai shirun tayi yawa ya Kamata ace zuwa yanzu yayi hakuri ya huce ya dawo gida". Ammin ta fada cikin damuwa. "Ba komai in Sha Allah lfy na fada Miki yanda mukayi da mustapha kema kince kina bibiyarsa ayi ta addu'a Allah ya sassauto da fushinsa ya waiwayo gida wallahi ko cikin dare yaron Nan ya Fadi min a Rai to barcina ya Kare Kullum ta Allah sai anyi mini saukar Alqur'ani akan Allah ya bashi kariya a duk inda yake wallahi nayi Dana sanin fada masa maganar da nayi danasan maganar tawa ze dauketa da zafi wlh da bazan fada masa ba yana cikin zafi". Hawaye ne ya balle Mata kamar lalataccen famfo har da shashhshekar ta. "Dan Allah Hajiya kiyi hakuri wlh ba maganar ki bace tasa yabar gida nakin dai yazo Kan gab'a ne kawai". "A'a keda Baki Nan mukayi yazo Nan Yana ta huci Dan motar dazo a ciki ma ko kashe ta baiyi ba ya fado min Kamar an jefo shi, Yana huci Yana Fadi wlh duk duniya ba Wanda ya Isa yasa ya auri safna Koda Matap sun kare shi Daman koya aureta biyayya ne zeyi Yana da wadda yake da muradin aure, ni kuma a lokacin bani da cikakken masaniyar abinda yake faruwa kinja layin kada a fada min gaskiyar maganar,Ina bude Baki sai ce Masa nayi idan ya ciki shi d'ane na halali ya shiga duniya ya Nemo min yarinyar da yake maganar a kanta Wanda take ganin darajarta tafi ta zuwairiyyar, wlh shiru yayi a inda yake tsaye kasa cemin komai yayi Kusan tsawon minti biyar, kafin ya kalli idona yace min wlh zakiga cikakken Dana halak, ki rubuta ki aje idan kin qara ganina a sokoto ba tare da ita ba to kuwa shege ne ni,idan Kuma ban sameta nida sokoto har abada ya juya ya wuce ko motar Bai kalla ba Kuma tun daga Ranar har Rana Mai kamar ta yau ban Kara saka mahmudu a idona ba, sai dai Babban yaronsa Yana zuwa ganina Yana kawo min duk abinda Mahmudun yake kawo min ciki kuwa harda magungunan da nake sha na hawan jini". Ammi tayi mamakin Jin Sameer na zuwa gurin Hajiyar koda Wasa Bata taba Jin haka ba, Kenan wato kafa ya bawa mutane Yana cikin Nigeria din kenan bawai inda ake zaton zashi ba. "Allah kyau Hajiya ki daina damun kanki, jikina Yana bani Yana cikin kasar Nan Kuma Yana da labarin komai tunda kikace min Sameer na zuwa, duk inda yake ya sani ya hana shi ya fada ne kinsan halin kayanki dai". Mardiyya da Urat Hajiyar ta kalla Tana fadin "yan nema kunki iyayenku sai uwar wasu tun barinki garin Nan yaran Nan suka tare a Nan Wai saina kaisu Yamai gurinki tunda aka fada musu naje suka tada hankalin iyayen sai su dawo Nan idan Zan koma na tafi dasu, Kinga mardiyya jiya da Iyayen sukazo daki ta gudu ta rufe Dan ma kada su tafi da ita, ko makaranta sai dai direban ya biyo ya dauke su anan ya dawo min dasu Nan". Kansu Ammi ta shafa tana fadin rigima ta kare tunda ga Ammin ku ta dawo ko?". Kai suka gyada Mata a tare. Masu aikin Hajiya ne suka shigo ta kofar baya daga kitchen suna fadin "lale marhabin da Ammi barka da zuwa". Gaisawa sukayi a mutunce tana tambayar su iyalansu. Abinci na musamman masu aikin suka gabatarwa da Ammi Wanda Hajiya ta hanasu sakat tun safe ake saukewa da dorawa da gaske Babu Mai shafewa Ammi Zane a gurin Hajiya tana sonta kamar me. Sai bayan insha'i Ammi ta kwashi su Urat ta nufi gida cikin motar data Bari a gidan Hajiyar. So take ta bada mamaki yanda ta fice batare da sanin kowa ba a wayi gari a ganta batare da kowa yasan sanda ta dawo ba, duk gidan amintacciyar Mai aikinta kawai ta Kira ta fada Mata tana Nan Zuwa garin yay ko su Abeeda ba Wanda ta fadawa tasan zumudin su ze saka kowa ya sani. ************ Safa da marwa take tun bayan gama wayarta da Aunty Ladi ranta idan yayi dubi a bace yake Wai shi wannan yaron wane iri ne aiki akeyi a kansa Amma Kamar ana zubawa a teku wannan guri na uku ne da Aunty Ladi taje Mata a Jos Amma amsar daya ce wannan yaron yafi karfinta, Mata ne guda biyu a teaye a kansa da addu'a sannan yana da tsarin jiki na ban mamaki Nan kusa ba abinda zeyi tasiri a kansa sai ikon Allah. Wayarta ta dauko Asabe ta Kira cikin k"an k'anin lokaci ta daga Kiran "kizo ina jiranki yanzu". Ta kashe wayar tayi wurgi da ita Kan gado. Cikin abinda bai wuce minti Sha biyar ba Asabe ta shigo gidan ko part din Ammah Bata shiga ba kamar yanda ta Saba direct ta wuce gurin Mama. Parlourn ba kowa ganin haka yasa ta wuce bedroom dinta a tsaye ta sameta tana kaiwa da kawowa Ido yayi Mata jawur kamar na tsohon mashayi. Ko sallamar ta Mama Bata ba ta amsa ba ta, fara fadin "Ina ne garin da kikace min 'yar dago kawarki ta fada Miki da wani shahararren mutum Mai aiki kamar yankan wuka?". Shigowa tayi ta zauna tana kallon mamar "Wai lafiya na ganki haka?" "Ina fa lafiya! Aunty Ladi ce ta tasheni daga barci take fada min taje har guri uku ba sa'a, Wai yanda suka fada Mata yanzu ne ma Zahra ta gamu da Wanda ake ta fada Mana a baya bawai wadanda mukayi ta aiki a kansu ba, Kuma Shi wannan din duk ya fisu Shirin jiki Dan da alama yanda sihiri baya tasiri a jikin ita yarinyar shima baya yi a jikinsa, Wai wasu Mata ne guda uku a da maza biyu tsaye a kansa duk juyi sihirin baya kaiwa inda yake, yanzu Kiran da nayi miki ina son Jin tabbacin kin koma kin tabbatar da Mai gadin ya saka wannan abubuwan da Kika bashi?". Dan murmushi tayi irin na kwararrun 'yan duniya din Nan kafin tace "Haba Hajiya shekara nawa muna tare ban taba ha'intarki ba sai yau an aiwatar da komai sai jiran sakamako kawai ai wannan yaron bama Azare ba Kasar Bauchin ma gaba daya shi da ita har abada, Kuma malamin da 'yar dagon ta fada min a wani gari yake cikin kasar katsina ana ce Masa Bakiyawa tace idan na shirya zata rakani garin iyayen mijinta ne daya rasu". Hake sukayi ta kullawa da kwancewa,Asabe nata Kara zugata akan ko nawa zata kashe kada ta Bari Ammah da 'yar zumunta su fisu komai, tunda ta Nan take samun nata rabon a jikinta idan Bata encouraging dinta itama zata rasa income nata. ** Tun bayan ganawa da Bakinsa Mahmud ya shige bedroom ya Haye gado yaso ya Kira Zahra suci gaba da Hira Amma saiya fasa Dan yasan yanzu gari ya waye sosai a 9ja Bari ya kyaleta sai dare hirar zatafi tafiya yanda yake so. Bai tashi ba sai lokaci sallah, wanka yayo ya saka kananu Kaya yayi sallah yana cikin addu'a yaji ana knocking din kofa umarnin shigowa ya bayar Sameer ne ya shigo Bakinsa yaki rifuwa. "Barka da Rana". Sameer ya fada Yana mikawa Mahmud wayar hannunsa. Hannu yasa ya karba yaga menene yasa shi irin wannan murmushin. Wani fine Baby ya gani nade cikin farin towel na jarirai fari sol. Kallon shi Mahmud yayi Yana neman Karin bayani. "Takwaranka ne madam ta haihu jiya cikin dare". Cikin madaukaikin mamaki Mahmud ya kalli Sameer "are you serious?" Kai ya gyada Masa Yana Fadin " yes sir". Mahmud sai juya wayar yake Yana Kara kallon babyn. "Masha Allah, my friend Allah ya Raya mana, amma me yasa ka taho ka baro yarinyar mutane a watan haihuwarta ai sai iyayenta suga rashin kyautatawar ka ga 'yarsu". Shafa Kai yayi Yana Dan murmushi "ba wani Abu,idan na zauna me zanyi musu duk abinda ake bukata nabar musu". Wani kallon baka da lfy Mahmud yayi Masa "an fada maka Bata bukatar kulawar ka ne a irin wannan lokacin?" wlh Dana San lokacin haihuwata yayi ba inda zakazo Kuma yanzu ka nemi visa ka koma gida daman Nan anyi clearing din komai U A.E din naji da komai kawai, naji kace takwara na nayi zaton sunan Abban koko za'a saka masa?". "Ai umarninsa ne yace nayi masa huduba da sunan ka". "To Masha Allah! Godiya ta har gida zanje na yiwa Abban tafi karfin ta waya Allah ya Raya Mana Mahmud yayi Masa Albarka, kaje ka Fara shiri tun yanzu ka shiga kasuwa kayi musu abinda ya Dace". "In Sha Allah". Godiya Sameer yayi ya nufi kofa Yana fita alarm na shigo Masa Wanda Saida ya girgiza shi baya yayo yana Murda kofar ze dawo ya jira yayi locking dinta, dariya yayi Yana Fadin "manya gatan Wasa, Allah ya biya maka bukatunka na Alkhairi". A Ranar cikin dare suka bar Kasar su duka Sameer yayi Nigeria shi Kuma Mahmud ya nufi U.A.E . ✨✨✨ AUREN HUCE HAUSHI. MAMAN FATEEMAH. Page 34 AssalamuAlaikum warahamatullahita'ala wabarakatuhu. 'yan uwa muna barar addu'oin ku bisa rashin abokiyar aiki da mukayi ECCD co-ordinator ta KIRIKASAMMA LOCAL GOVERNMENT JIGAWA STATE muna rokon Allah s.w.a ya jikaanta yayi Mata Rahama yasa Aljanna makomarta tare da Iyayen mu da sauran Al'ummar musulmi Baki daya ya Raya abinda ta Bari ya Albarkaci bayanta. ______ Misalin karfe uku da rabi jirgin sun Mahmud ya sauka a DUBAI INTERNATIONAL AIRPORT (DXB) cikin amincin Allah, yana cikin kusan rukunin mutanen karshe a fitowa, yana sanye da suit ash colour na kamfanin Armani hannunsa sanye da ogogo Rolex, baya tare da komai sai jakar laptop dinsa a hankali yake gangarowa cikin takunsa na cikakken namiji me ji da lafiya da karfi, direct gurin da taxin airport suke ya nufa, baya bukatar asan yazo garin so yake ya tantance wata jimurda da aka hada, taxin ya shiga saida sukayi balance a titi sannan ya fadawa direban ya kaishi JW moritte marquis hotel cikin harshen larabci,sunyi tafiya mai tsayi kafin su karaso hotel din, bashi da matsalar kama daki dan tun yana china yayi booking din dakin ta online, katin dakin kawai ya karba ya koma waje yin 'yan uzurirrika daga baya ya nufi ciki, wanka ya fara kafin yayi order abinci, sai da ya gama komai sannan ya kwanta dan yayi matukar gajiya, yaso kwarai ya kira 'yar gidansa amma yana son su tattauna sosai, sai yanzu yake jin haushin wani ra'ayin nasa badan haka da suna tare da ita suna hutawarsu, yanzu kadaicin rashinta da be dameshi ba, wlh da beyi alkawari ba da visa zesa ayi mata ta sameshi a nan saboda hotel din yayi masa, yana daga cikin lattest hotels na duniya be taba sauka a wani hotel ba a dubai sai BURJ AL ARAB JUMAEIRAH dakinsa parmanent ne duk mai hulda dashi a dubai nan suka sani, duk da yana da gidaje a kasar shi be fiye son yakai abokanin bussiness dinsa gida ba. Wannan shigar ta sirri ce shi yasa ya canza sheka baya son asan ya shigo kasar mamaya sake son yakai wasu gurare, yanda har ya gama abinda yake yabar kasar wani be sani ba duk da abune mawuyaci hakan ta faru. Barcinsa yasha sosai dan har akayi sallar magariba be sani ba, lokacin daya tashi ana gab da kiran sallar insha'i, a gurguje yayi wanka ya zura sabuwar jallabiyar daya saya cikin kayansa a kasar, a cikin dakin yayi sallar magariba ya fito yabi lifter zuwa masallaci,koda suka idar da sallah be dawo daki ba a nan harabar hotel din ya Zauna da gaske yanayin gurin ya burge shi sosai, coffee yayi order ba'a jima ba wata matashiyar balarabiyar yarinya ta kawo masa coffeen sai yaga kamar 'yar gidansa, nan da nan yaji duk rintsi ita yake muradin gani number dinta ya lalubo ya kira duk ba baya son kira direct yafi son ta Whatsapp. Suna zaune a parlour ita da zilai tana Shan mutuniyar tata farm fresh, Kira ya shigo a wayarta dake kusa da ita, tayi mamakin ganin code din Dubai har sai da ta kusa katsewa sannan ta dauka, batayi magana ba Shima baice komai ba, ganin shirun yayi yawa yasa zilan Fadin "naji kinyi shiru koba Kira bane". Karamin tsaki Zahra tayi "wlh na daga amma naji shiru inaga ko wrong number ne dan code din na Dubai ne ni kuwa waye ze kirani daga Dubai da dai Aunty Nawwara Bata saudiyya da saina dauka ko sunje ne da mijinta tunda business man ne, Bari na kashe wata kilama ba'asan an Kira ba".. Kafin ta dauke wayar daga kunnen ta taji yayi magana cikin husky voice kada ki kashe min waya, ki bude data zamuyi magana". kit ya kashe Kiran wayar tabi da kallo a zuciyar ta tana Fadin "ikon Allah shine Kuma a Dubai ya illahiy, to Wai wannan Dan talikin waye shi lamarin fa Yana neman Zama abin tsoro fa, yace Yana yiwa kungiyoyin waje aiki ita Kuma a gefe guda wani Abu yake yi irin na Mai bada umarni Kuma bataga yanayi gaban kowa ba sai ita, kamar Ranar da taji yana Kiran zayyan da umarnin daya Bashi akan lallai ya sameshi da safe Kuma Bai karya Umarnin ba" Wayar ta kalla tana mikiwa zuwa bedroom dinta Saida ta shiga ta duba data idan Babu ta saka tunda Sam Bata taba saka data ba tunda ta Fara amfani da wayar datar data gani tayi bala'in Bata mamaki 4.5 BT ta gani sub din shekara daya ne. Cikin sofa ta zauna Tana juya wayar Bata bude datar ba, wani Kiran ne ya sake shigowa still dai nashi ne, dagawa tayi tana fadin Assalamu Alaikum warahamatullahi ta'ala wabarakatuhu". "Wa'alaiki Salam warahamatullahi ta'ala wabarakatuhu, meya hanaki bude datar danace a bude?" Shiru tayi ta kasa magana,. "Wai ko sai nayi ramuwar sayen bakin da banyi bane ake min jan aji irin haka. Dan Allah kimin magana kona samu nutsuwa wlh ji nakeyi Kamar na gudo tun ba'a gama ba duk kin mamaye ko Ina na kasa komai sai tunanin ki, Ni danasanin zuwan ma nakeyi gashi sun rarraba mu wasu suna London mu kuma suka kawo mu hadaddiyar daular larabawa, shine nace Bari na kira na fada Miki Koda abinda kike bukata na taho Miki dashi tunda da kudinki a gurina" "Kudina kuma? Name nene kuma yaushe na baka". "Bake Kika bani ba ke aka bawa na manta na Baki Sai a Nan na tuna danaga Kaya irin naku na 'yan Mata". Ya fada Yana dariya. "Wai 'yan Mata". Ta fada tana Dan turo Baki irin bataji dadin Nan ba. "Au ashefa an wuce wannan stage din ko?" Ya fada da alamun zolaya. "Wato kinki bude data sai kin cinye min 'yan canjin da aka saka Mana kinsan dai ni ba iya saka Kati zanyi a kasar Nan ba, pls Dan Allah ki bude datar na ganki kona samu nutsuwa nayi aikin daya kawoni, naso ace kina gefena a wannan gurin Kinga dakina kuwa? da Hali gareni anan zamuyi honey moon irin Wanda naji su Habib suna fada idan ana hira ko Zaki biya ki taho ki sameni?" Ido ta ware kamar Yana kallonta. "Na biyoka nayi maka menene?" "Kiyi min abinda mace take yiwa mijinta ai kin gane?". "Ya Salam haba Ya Mahmud menene haka kaifa yayana ne". Wata dariya ce ta kubce Masa "A yaushe na zama Yayanki? Ki gyara zancen niba Yayanki bane, haka kawai ki haramta min abinda Allah ya halasta min idan Zaki Ware ki Dan ina dawowa labarin ze canza salo gara mu fuskanci juna ki tausaya min Kinga Sameer fa ya Zama Daddy madam dinsa ta haihu sunyi min takwara,ai gara muma mu zage dantse ko?" Dokin haihuwar da aka fada Mata ita ta Hana ta gane inda nasa zancen ya dosa, cikin nuna farin ciki tace "Dan Allah da gaske yaushe Fateehar ta haihu? Masha Allah! Allah ya Raya kace mu sai Kano ko Yaya?". "Allah bakinki ya kiyayi fada min yayan Nan tsabar kinibibi kawai yau Kika tashi dashi Wai wani Yaya kamar a kauye, kibar 'yan garinmu su Fadi Amma Banda ke wato Ni da yake ba Dan bokon kirki bane ba baza'ace min sweetie ba ko irin su my love ko Dear, saboda almajirin soro ne ni ko?" "A'a wlh ni ban fada ba, kawai dai Naga abokin Ya Abdul Hakeem ne kai ai kaima yayan ne". "To anki wayon, Kuma da kike cewa Zaki Kano ganin yaro keda wa zakuje kuma waye ze kaiki Kuma kice Mata wacece ke". "Address zata turo min Mana, Kuma maganar kaiwa sai Malam Bala direba kaimu nida mujiba wuni daya dai, Kuma nace Mata matar yaron mijinta ce ko ba haka ba? "Yayi Kam Amma saina dawo ki rakani muje tare anfi saurin ganeki ga kafarki ga tawa, kice na sawo Miki kayan baby na zuwa barka kenan? ko kema a hado Miki kayan naki babyn? tunda da karfina Zan dawo wata kilan ni double shoot ma zanyi tunda Nima Dan biyu ne Ina da twins sister Aishat". "Twins sister da gaske?" "Kin taba ganin nayi Miki karya? wlh mu biyu Ammin mu ta haifa first born dinta, mun B'ata ne da ita shiyasa bakisanta ba. Amma nan gaba zaki santa ne Amma fa Zaki Sha surutu Dan sister Aishat parrot ce". "Amman laifin me tayi maka da zafi haka? Mu namu twins din basa doguwar batawa gaskiya gashi kaima Ammin irin na Ammah tayi mace da namiji". "Ki Bari kawai labarin da tsawo sai na dawo ai nace Zaki San duk labarina kaf ba abinda Zan boye Miki tunda kin sarkafo min zuciya tun kina free matured dinki Kika Hana duniyata zaman lfy,da farko na dauki irin mutum ya burge ka ne Ashe diban Karan mahaukaciya Kikayi da gudan tsokar kirjina". Dariya maganarsa ta bata. "Au dariya ma kike min ko? bayani zakiyi da yarenki, yanda nayi ta fama da garari saina fanshe kayana tas idan Zaki shirya ki shirya". Cuno Baki tayi kamar tana gabansa ta Fara turza kafa tana fadin "Ni yaushe kaga Ina maka dariya kawai dai... ni banyi maka dariya ba kaifa yayana ne koka manta my big bro....." Ta wani ja cikin salon da ita kanta Bata San tayi ba. "Ya salam" ya fada a hankali Dan yanda tayi magana har cikin bargonsa. "Kinaso ki karya min budget ko?" Ya jefa Mata tambayar. "Wane irin budget Zan karya maka kana Nan Ina Nan". "Idan kina min irin haka ai sai kisa na saki layin Dana hau na tattaro ya nawa ya nawa ko komo gida ko ba'a gama ba". "To me nayi daga magana tom shike Nan sai anjima". "Wlh Kika kashe min Kira sai kinzo Dubai ko a kafa ne kuma saina yi Miki abinda bazaki manta ba Dan tarihi me kyau Zan kafa Miki ki kashe ki gani, muna hira kina bani nutsuwa Zaki gudu nida ake yashewa Yan canjina Baki tausaya min ba shine Zaki tsere ki barni da Mata masu farauta ta ko? Yanzu haka guda uku tun dazu suke shawagi a gabana suna tunanin irin nasu ne Dan hannu". Gyara Zama Zahra tayi kirjinta ba dukan tara tara bama uku uku ba. "Mata kace ko me?" "Eh Mata Mana bake kina min rowar ganin halalina ba to gashi Nan free sai Wanda yayi maka ka zabi son ranka, ba nace ki bude data na kalli kayana ba Amma kika Kiya Kinga kuwa yanzu saina duba na darje na zaba ta rage min dare, koya kikace my previous?" Ya Dana Mata kiss ta cikin wayar ya kashe abarsa. Yana fadin gobe ma idan bace ki bude datar ki qiya, saina kowa Miki kishina ba gaske kafin na kaiki Ina zakiyi da hujja Amma ki shiga yanzu ai Africa ce da sauran gyara. AUREN HUCE HAUSHI MAMAN FATEEMAH PAGE 35. ________Yana katse Kiran ya tashi tsam ya nufi masaukinsa laptop dinsa ya janyo ya shiga aiki sai kusan karfe daya ya kwanta lokaci bayan lokaci sai yayi murmushi idan ya tuno yanda suka rabu da 'yar gidansa yayi zance mata tana neman tikitawa kanta lissafi Wai ita me miji, kamar ta wani san dadin mijin,Saida yayi wanka yayi nafila sannan ya kwanta. * Zahra kasake tayi da waya a hannu kamar itace Mahmud din "me yake nufi da zasu rage Masa dare kenan neman Mata yajeyi?" Take wata zuciyar tace Masa A'a Yana zolayarki ne da manemin matan ne koda karfin tuwo saiya nemi wani Abu a jikinki, kauda wannan tunanin tayi daga zuciyar ta tasan zato zunubi ne, parlour ta koma gurin zilai sukaci gaba da hirarsu sai kusan Sha daya suka shiga ciki. Washe gari Zahra Bata tashi da wuri ba sai kusan Sha daya, tun cikin dare bata Jin Dadi wata irin murdawa mararta ke Mata, tana samun irin wannan pain din duk karshen wata idan zatayi period Amma wannan yanda yake mata yayi tsanani sosai tun wurin karfe ukun dare ciwon ya tashe ta farka a gigice, inda Allah ya taimaketa Bata sakaci ta rasa maganinta duk rintsi Yana tare da ita, a lokacin ta sha cikin ikon Allah lokaci kalilan ciwon ya lafa ta koma barci da Asuba ma data tashi sallah da sauki sosai sai Kuma yanzu data farka taji Yana neman dawo Mata, da kyar tayi wanka ta sake inner wears ta zura rigar matarial marar nauyi ta koma ta kwanta idan tana wannan yanayin ko turare Bata so sai guda daya kawai body mist ne na strawberry shi ta fesa ta koma ta kwanta Dan abinci dai baya ciyuwa a irin wannan yanayin. Ganin Sha biyu tayi Zahra Bata fito ba yasa zilai nufar bedroom din nata ta gani anya lafiya kuwa? Knocking tayi taji Shiru ta qara you taji Shiru Bata kara ba uku ba ta tura kofar a can tsakiyar gadon ta ganota a kudundune, da sauri ta karasa gaban gadon tana ambatar sunan ta "Zahra kafiyarki kuwa har Sha biyu ta gota Baki tashi ba abin Karin ki har ya Fara sanyi?" Da kyar ta dago ta kalli zilan cikin miryar marar lafiya tace Mata "bana Jin dadi tun cikin dare marata take ciwo". "Subahaballahi Kuma Kikayi Shiru Baki fada ba idan haka ne bani da amfani Kenan ace tun cikin dare kina fama da ciwo ki kasa fada mini, ina maganin da kike Sha yake na dauko Miki Ni wlh cewa nake tunda ance idan Kikayi aure ze dena, to na dauka kin rabu dashi yanzu, ai haka wannan likitar ta fada Miki zuwan mu na karshen ko?". Kai Zahra ta gyada Mata kawai alamar Eh Dan ita kadai tasan azabar da takeji. "Fada min Ina maganin yake na dauko Miki" A hankali tace mata "Na sha". "Kin sha Kuma marar Bata Dena ciwon ba?" "Eh" ta fada tana runtse ido saboda azabar ciwo. Fita zilai tayi da sauri ta koma dakin da aka sauketa ta lakubo keyboard dinta ta lalubo number Ammah, lokacin tana tare da Abba suna maganar komawa makarantar Imam Kiran zilan ya shigo. "Abba Bari na daga Kiran Nan Zilai ce naji ko lafiya". "In Sha Allahu ma lfy". Abban ya fada. "Assalamu Alaikum warahamatullahi ta'ala wabarakatuhu" Ammah ta fada bayan ta daga wayar daga can zilan ta gaishe da Ammah sannan ta Dora da fadin "wlh Ammah jikin Zahra ne ba Dadi tun cikin dare ciwon mararta ya tashi Tasha maganin Kuma a banza shine nace Bari na Kira na fada Miki Koda abinda zakiyi mata tunda kema Aikinki ne ko Kuma a turo Mana malam Bala ya kaimu Asibiti taga likitar ta" . "Ikon Allah! Yanzu ina zahrar?". "Tana daki tana faman mukususu kamar me nakuda wlh abin gwanin ban tausayinsa". "To shike Nan ki dubata za'a San yanda za'a yi ki jira". Ta kashe wayar ta dubi Abba Wanda Shima itan yake kallo, kafin tayi magana ya rigata. "Meya samu Uwata naji Kuna magana Bata da lfy ne?" Ajiyar zuciya Ammah ta sauke "wlh ciwon mararta ne Wai ta tashi tun cikin dare Tasha maganin da take Sha Amma ba wani cigaba shine zilan tace ko Asibiti zasu koma suga likitar da take gani Dan munyi expecting idan tayi aure zasu rabu to Kuma a yanda zilai ta fada min kamarma yafi na baya zafi". "Ikon Allah! Allah ya saukake Bari a tura musu magaji ya kaisu Asibitin tunda duk sauran basa Nan sai mu bisu daga baya mu kuma, ai hakan yayi ko?". Kai ta gyada Masa tana kokarin tashi da nufin tafiya, riko hannunta yayi ya mayar da ita inda ta tashi dayan Kuma Yana Kiran wayar magaji. "Ka dauki mota kaje can hayin banki zaka Kai uwata Asibiti". Ya kashe Kiran yana kallon Ammar. "Ina zaki Kuma Kika tashi? Ki kwantar da hankalinki in Sha Allah ba wata damuwa Kika sani ko jika zamuyi kwanan nan" Ya fada Yana dariya irin tasu ta manya. Itama Dan murmushi tayi tana fadin Allah yasa". "Amin yauwa kokefa dauko gyakenki mu bisu wata Kila muje tare tunda gani a gida araha sai nayi aikin bariki tilas ne". Zilan Ammah ta Kira ta fada mata su shirya ga magaji Nan ze kaisu Asibitin, Suma zasu samesu a can.. Dakin Zahra zilan ta koma yanda ta barta haka ta sameta, kusa da ita zilan ta matsa tana fadin na hado Miki ko ruwan shayi ne kisha Asibiti zamu". Kai ta girgaiza Mata alamar bazata Sha ba. "Ki daure ko kadan ne Dan Allah Kinga wata Kila ayi Miki allura gara kici ko kadan ne". "Cornflakes". Abinda ta iya fada Kenan ta koma ta kwanta. Ba laifi tasha cornflakes din da Dan dama, rolling kawai tayi suka nufi parlour zilai na rike da ita. Basu jima ba sukaji dirin mota alamar magajin ya karaso Kenan, zilaice ta bude kofar tun Bai karaso ba direct inda zahrar ke kwance ya nufa akan two seater. "Sannu Adda ya jikin naki?" Da kyar ta cira Kai ta dubeshi tana fadin "da sauki". "Allah ya Kara sauki, kamota muje kada Rana ta karayi yanzu twenty five minutes to one fa". Zalai ta riketa tana tafiya da kyar suka fito compound din Zayyan yana zaune Yana game a waya tunda bashi da aikinyi a Nan sai zama,ba zato yaga an fito da Zahra haka, da sauri yayi wurgi da wayar Allah ya taimake kan jacket dinsa ta fada da sai dai wata ba ita ba, ya nufo gurinsu Yana tambayar "Lafiya meya faru? Oga kuwa ya sani? sannu" duk a lokaci daya yake jero wadannan tambayoyin da gani a rude yake. Magaji ne ya nufi inda yake suka Kara gaisawa Yana farin. "Ba wani abun damuwa bane Bata Jin Dadi ne zamuje Asibiti kada ka damu". Zilai magajin ya duba "kun fadawa mujinta kada mu tafi babu sanin sa". "A'a bamu fada Masa ba ai ko daga bayane an fada Masa yanzu dai muje Asibitin wannan ma wani Bata lokacin ne". Da sauri Zayyan ya bude musu gate suka fita yayin da Zayyan din ya dauko wayarsa Yana Kiran Mahmud. Ya kirawo shi Amma Sam taqi shiga sai text kawai Zayyan ya tura Masa ya koma ya zauna yana mamakin ogan nasa na neman gurin Zama a wannan Dan gurin shi ko takura ma yaga alama bayayi wata sabuwar rayuwa yake shimfidawa cikin kwanciyar hankali. Direct A&E magaji ya nufa zilai ce ta taimawa Zahra ta fito daga mota suka shiga ciki shi Kuma magaji ya nufi inda ze karbo file. Ba jimawa yazo ya kawo file din, bayan duguwar tambayar da wata likita da take on call tayi Mata ta rubuta Mata magunguna da allurai da drip ana cikin saka Mata ruwa su Ammah suka shigo dakin, ma'aikatan da masu jiyyar suna ta gaishe da Abba, gaban gadon Abban yaje ya tsaya sunan ta Abban ya Kira ta bude Ido ta kalli Abba tana kokarin tashi zaune "A'a uwata koma ki kwanta ya jikin naki?" "Da sauri Abbana, Ina kwana?" "Lafiya kalau". Ammah ce ta matso tana fadin "sannu Ashe ciwon cikin ne ya tashi?" "Eh Ammah wlh har yafi Wanda nakeyi kamar Zan mutu". Ta fada tana goge hawayen daya zubo Mata. "A'a uwata Banda kuka ai kin girma". Abba ya fada Yana dariya. Itama Zahra dan murmushi tayi ta juya Kai kunya ta kamata ta. Abba Bai bar Asibitin ba Saida aka Maida Zahra Aminity ward. Tun bayan tafiyar su Zahra Zayyan ya kasa tsaye ya kasa zaune, ya nemi number Mahmud tafi cikin carbi amsa daya balarabiyar da akayi linking da computer ke bashi wadda ba fashimta yake ba, sai dai hasashe kawai number Bata tafiya take fada Masa. A gida Abba yayi sallar Azzahar bayan an fito ne ya fadawa Baba malam Zahra tana Asibiti Bata Jin Dadi. Cikin nuna jimami Malam yace "tun yaushe take Asibitin ba'a fada min ba, kuma menene yake damun diyar tawa?". "Wlh ciwon cikin ne take fama dashi tun cikin dare shine dazu Mai Taya ta Zama ta kita Asma'u ta fada mata, sai nasa magaji ya Kai su Asibitin sai suka Bata gado Wai zasuyi Mata hoton cikin da sauran gwaje-gwaje don su fadada bincike akan ciwon tunda ta jima tana fama da lalurar". "Ikon Allah! Allah ya Bata lfy yasa kaffara ne, ai da anyi magana tun a bayan da an Nemo Mata taimakon ciwon Amma yanzu ma Bata baci ba, idan anyi binciken an gano wane irin ciwo ne a fada mini akwai magungunan ciwon cikin Mata da yawa a gurina in sha Allah koda tsiron mahaifa ne da sauransu in Sha Allah zasu narke Koda na aikine zebi jinin al'ada ya narke ya zube". "To in Sha Allah Zan fadawa Asma'u kome Kenan Zan fada maka". Sun jima a harabar gidan Abban kafin suyi sallama. Bayan sallar la'asar malam yasa Habib ya tukashi zuwa Asibitin lokacin da sukaje Zahra tana barci sun gaisa da Ammah Malam ya jajanta Mata Habib ma ya jajanta Mata jikin Zahrar Basu dade ba suka tafi. **** Tun safe da Mahmud ya fita tare da daya daga cikin amuntattun hadimansa na kasar suka fice sun Kai ziyarorin bazata Dan tono wasu laifuka da ake son binnewa, ya dakatar da mutum hudu ya sallami mutane biyu wadanda sukayi sama da fadin maqudan kudade tun bayan rashin sanin inda Mahmud din yake ganin tafiya tayi nisa Kuma baya bibiyar su Sam sai kawai suka tsunduma cikin dukiyar sukayi dumu dumu a ciki, zuwan Sameer ne ya bankado badaqalar wadda tafi karfin shi wadda tasa dole Saida Mai takanas din ya taso, China Kuma issue ne na rufe musu kamfanin laces da materials da akayi Wanda suke zargin ba'a biya kudin harajin kasa ba a tun farkon bude kamfanin, Mahmud yayi kokarin tura duk evidence dinsa ta wibeside nasu Amma sunqi yarda Wanda dole tasa Saida yazo da kansa sannan lamarin ya gyaru. Sai dare sosai ya dawo masaukinsa yaso ya fita ya dan shaqata beach Amma yayi matukar gajiya sosai Koda yayi wanka coffee kawai yayi order da snacks, tunda garin Allah ya waye Bai samu kanshi ba sai yanzu wayarsa ya dauko ya kunna Dan rabon da ya kunna ta tun jiya, sakonni ne suketa shigowa rututu, amma na Zayyan da Habib su sukafi daukar hankalinsa lfy? Ya tambayi kansa. Sakon Zayyan ya fara budewa ai baisan lokacin daya Mike tsaye ba duk gajiyar dake tare dashi Nan take tayi nata guri, cikin tashin hankali ya Fara lalubar number din Zayyan cikin kankanin lokaci Kiran ya shiga, Bai saurari gaisuwar da yake Masa ba ya Fara fad'in "wace irin magana kake min haka? Ashe ajiyekan da nayi bashi da anfani,tun safe Amma kaqi fada min halin da yarinyar mutane take ciki sai yanzu da tsohon Daren nan? Kana son ace ban damu da halinda 'yarsu ke ciki ba tunda throughout yau ban kirata ba nayi busy sosai".."sorry oga wallahi tun lokacin nake neman wayar ka Bata shiga kwata kwata shine nayi make text". "Oh shit! Wlh ban bude wayar ba sai yanzu, yanzu ina zahrar?" "Wallahi Yallabai bansan inda take ba tunda suka fita ban Kara samun wani information akan komai ba". Tsaki Mahmud yayi ya datse kiran. Habib ya lalubo ai sakonma bai tsaya dubawa ba ya Kira shi. "A gaggauce ya amsa sallamar da gaisawar da Habib din yake Masa. "Wai meke fatuwa ne da Zahra?". "Wallahi Nima bani da masaniyar takamaimai kawai dai bayan anyi sallah baba Malam yace na kaishi Asibiti ya gano jikinta sai a lokacin na Sami labarin Bata da lafiya ance ciwon ciki ne, lokacin da mukaje tana barci Amma idan an jima zan koma na qara dubota kome kenan Zan fada maka ka kwantar da hankalinka naji Abban su Yana fadin Daman tana fama dashi ne Saida na yau yafi zafi fiye dana bayan gaskiya Dan har hoto da gwaje-gwaje zasuyi Mata inga in Sha Allah ba wani damuwa kome ake ciki Zan sanar da kai Allah ya Bata lafiya". "Allahumma Amin". Ya fada jikinsa a mace da duk ya shiga cikin damuwa. Number zahrar ya Kira tana ta ringing Amma ba'a dauka ba tsaki yayi tunda yaji haka yasan wayar na gida Basu dauka ba. A karo na farko ya Kira wayar Ammah lokacin wayar na hannun Auta Wanda ya biyo mama da Asabe Asibitin, Dan lokacin da su Ammah suka taho mamar Bata Nan Wai taje duniyar kanwar Babar su Asaben, shine da suka dawo.Abba ke fada Mata Zahra ba lafiya suka taho harda Auta, Autan dake kusa da Mama da wayar Amman a.hannu Yana game na football Mamar dake kusa dashi ta karbi wayar ta mikawa Ammah, batare da Ammah ta duba wayar ba ta daga tana fadin. "Assalamu Alaikum warahamatullahi ta'ala wabarakatuhu". Cikin girmamawa Mahmud ya fara gaishe da Ammah, ita har ga Allah Bata tab'a kawo Mahmud ze Kira ba. Dan Jim yayi Yana Jin nauyin tambayar ta Zahra, Jin shirun yayi yawa bayan gaisuwar yasa Ammar fadin "wa ake nema ne". "Ammah nine na kirane naji ya jikin Fateemah? wlh ban sani ba tun safe ban bude wayar ba muna aiki sai yanzu dana bude ake fada min Bata da lafiya Kuna Asibiti, Dan Allah ayi hakuri in Sha Allah hakan bazata fatuwa ba". Ammah ji tayi kamar ruwa ya cinyeta Ashe sirikinta ne wlh Sam bata Gane shi ba. Ciki Jin kunya da Kara Ammah tace Masa "ba komai ai jikinta da sauki yanzu ma barci takeyi, ya akayi suka fada maka haba ka kwantar da hankalinka Daman takanyi irin wannan ciwon lokaci lokaci sai dai wannan ne ya Dan matsa Mata sukayi admitting din ta zasu bincike a Kai". Ammar ta fada tana dan jin nauyinsa. "To Ammah nagode in Sha Allah da safe Sameer ze shigo zasuje Kano Nan Aminu Kano zasu dubata sosai tunda suna da Gynecologist consultant Ina ga kamar hakan zaifi can suna da kayan aiki na zamani, Zan Kira Abba da Baba Malam muyi maganar, na gode Allah ya Bata lafiya". "Allahumma Amin, Allah ya bada sa'a yayi Albarka". Sukayi sallama. Bayan sunyi sallama Ammah wayar tabi da kallo tana mamakin yanda yake magana da ita tamkar mahaifiyar shi, ya kama sunanta radau. Mama ce ta kalli Ammah tana fad'in "ko mijin nata be? Naji kina masa bayanin yanayin ciwon nata gashi abin takaicin tun ba'aje ko Ina ba ya tsallake ya bar yarinya da wahala, Allah dai yasa ba juduwa yayi ba ya barta da jangwam yanda aka Fara 'yan ciwace ciwacen Nan ai karshen maganar ace ciki ya bayyana shi Kuma yayi masa wuri tunda Daman tsintacciyar magen ce Bata mage ya sulale yabar gari naji ance harda motarta ya tafi Kinga ribar kafa Kenan". Duk surutun da Mama keyi akan Zahra ko kallon ta Ammah batayi ba Dan tasan tana fada ne dan ta Bata Mata Rai kawai, Zilai ma Mai aikin su tana tsaye kusa da Zahra tana gyara Mata hannunta da aka saka mata drip, itama ko tari be kunce Mata ba bata tofa tata ba, to me zata ce maganar ba ta ta bace. Jin ba Wanda ya tofawa Mama ko A a cikin maganarta yasa Asabe cewa. "Wallahi kuwa mama Allah abin tsoro mutum abin tsoro daman nasan in ba wani ikon Allah ba yaron Nan guduwa zeyi yayi gaba kinsan irinsu Yan hujja ne ba wani Zama zeyi na din-din-din ba a garin Nan, abin gudun ma ya jonawa yarinya ala kakai ya tafi ya barta da 'ya'ya, Kuma ki duba kiga yaro Nan a wanke yake Kar bashi da duhun jahilci ko kauyenci ko qanqani haka kawai ya jonawa yarinya alakakai ya gudu ya barta, idan tafiya ta Mike wata Ranar har azo ana yiwa yaro gorin mahaifi ga babu jinjinan dangi kana ji a sheganta yaro ko yarinya". Har Zilai ta baro bakin gadon da zimmar maida martani, sai maganar Zahra suka juyo suka juyo tana kallon Asabe Tana fad'in "lafiya kalau muka rabu, bai Kuma bar garin Nan ba Sai da ya fada min salinsa da iyayensa daga karshe ma mutum ya aje min saboda yana yin rayuwa koda ta Allah ta kasance shine ze kaini har dakin mahaifiyar sa Kinga kuwa ai bani da damuwa a Kan lamarin". AUREN HUCE HAUSHI MAMAN FATEEMAH PAGE 35. ________Yana katse Kiran ya tashi tsam ya nufi masaukinsa laptop dinsa ya janyo ya shiga aiki sai kusan karfe daya ya kwanta lokaci bayan lokaci sai yayi murmushi idan ya tuno yanda suka rabu da 'yar gidansa yayi zance mata tana neman tikitawa kanta lissafi Wai ita me miji, kamar ta wani san dadin mijin,Saida yayi wanka yayi nafila sannan ya kwanta. * Zahra kasake tayi da waya a hannu kamar itace Mahmud din "me yake nufi da zasu rage Masa dare kenan neman Mata yajeyi?" Take wata zuciyar tace Masa A'a Yana zolayarki ne da manemin matan ne koda karfin tuwo saiya nemi wani Abu a jikinki, kauda wannan tunanin tayi daga zuciyar ta tasan zato zunubi ne, parlour ta koma gurin zilai sukaci gaba da hirarsu sai kusan Sha daya suka shiga ciki. Washe gari Zahra Bata tashi da wuri ba sai kusan Sha daya, tun cikin dare bata Jin Dadi wata irin murdawa mararta ke Mata, tana samun irin wannan pain din duk karshen wata idan zatayi period Amma wannan yanda yake mata yayi tsanani sosai tun wurin karfe ukun dare ciwon ya tashe ta farka a gigice, inda Allah ya taimaketa Bata sakaci ta rasa maganinta duk rintsi Yana tare da ita, a lokacin ta sha cikin ikon Allah lokaci kalilan ciwon ya lafa ta koma barci da Asuba ma data tashi sallah da sauki sosai sai Kuma yanzu data farka taji Yana neman dawo Mata, da kyar tayi wanka ta sake inner wears ta zura rigar matarial marar nauyi ta koma ta kwanta idan tana wannan yanayin ko turare Bata so sai guda daya kawai body mist ne na strawberry shi ta fesa ta koma ta kwanta Dan abinci dai baya ciyuwa a irin wannan yanayin. Ganin Sha biyu tayi Zahra Bata fito ba yasa zilai nufar bedroom din nata ta gani anya lafiya kuwa? Knocking tayi taji Shiru ta qara you taji Shiru Bata kara ba uku ba ta tura kofar a can tsakiyar gadon ta ganota a kudundune, da sauri ta karasa gaban gadon tana ambatar sunan ta "Zahra kafiyarki kuwa har Sha biyu ta gota Baki tashi ba abin Karin ki har ya Fara sanyi?" Da kyar ta dago ta kalli zilan cikin miryar marar lafiya tace Mata "bana Jin dadi tun cikin dare marata take ciwo". "Subahaballahi Kuma Kikayi Shiru Baki fada ba idan haka ne bani da amfani Kenan ace tun cikin dare kina fama da ciwo ki kasa fada mini, ina maganin da kike Sha yake na dauko Miki Ni wlh cewa nake tunda ance idan Kikayi aure ze dena, to na dauka kin rabu dashi yanzu, ai haka wannan likitar ta fada Miki zuwan mu na karshen ko?". Kai Zahra ta gyada Mata kawai alamar Eh Dan ita kadai tasan azabar da takeji. "Fada min Ina maganin yake na dauko Miki" A hankali tace mata "Na sha". "Kin sha Kuma marar Bata Dena ciwon ba?" "Eh" ta fada tana runtse ido saboda azabar ciwo. Fita zilai tayi da sauri ta koma dakin da aka sauketa ta lakubo keyboard dinta ta lalubo number Ammah, lokacin tana tare da Abba suna maganar komawa makarantar Imam Kiran zilan ya shigo. "Abba Bari na daga Kiran Nan Zilai ce naji ko lafiya". "In Sha Allahu ma lfy". Abban ya fada. "Assalamu Alaikum warahamatullahi ta'ala wabarakatuhu" Ammah ta fada bayan ta daga wayar daga can zilan ta gaishe da Ammah sannan ta Dora da fadin "wlh Ammah jikin Zahra ne ba Dadi tun cikin dare ciwon mararta ya tashi Tasha maganin Kuma a banza shine nace Bari na Kira na fada Miki Koda abinda zakiyi mata tunda kema Aikinki ne ko Kuma a turo Mana malam Bala ya kaimu Asibiti taga likitar ta" . "Ikon Allah! Yanzu ina zahrar?". "Tana daki tana faman mukususu kamar me nakuda wlh abin gwanin ban tausayinsa". "To shike Nan ki dubata za'a San yanda za'a yi ki jira". Ta kashe wayar ta dubi Abba Wanda Shima itan yake kallo, kafin tayi magana ya rigata. "Meya samu Uwata naji Kuna magana Bata da lfy ne?" Ajiyar zuciya Ammah ta sauke "wlh ciwon mararta ne Wai ta tashi tun cikin dare Tasha maganin da take Sha Amma ba wani cigaba shine zilan tace ko Asibiti zasu koma suga likitar da take gani Dan munyi expecting idan tayi aure zasu rabu to Kuma a yanda zilai ta fada min kamarma yafi na baya zafi". "Ikon Allah! Allah ya saukake Bari a tura musu magaji ya kaisu Asibitin tunda duk sauran basa Nan sai mu bisu daga baya mu kuma, ai hakan yayi ko?". Kai ta gyada Masa tana kokarin tashi da nufin tafiya, riko hannunta yayi ya mayar da ita inda ta tashi dayan Kuma Yana Kiran wayar magaji. "Ka dauki mota kaje can hayin banki zaka Kai uwata Asibiti". Ya kashe Kiran yana kallon Ammar. "Ina zaki Kuma Kika tashi? Ki kwantar da hankalinki in Sha Allah ba wata damuwa Kika sani ko jika zamuyi kwanan nan" Ya fada Yana dariya irin tasu ta manya. Itama Dan murmushi tayi tana fadin Allah yasa". "Amin yauwa kokefa dauko gyakenki mu bisu wata Kila muje tare tunda gani a gida araha sai nayi aikin bariki tilas ne". Zilan Ammah ta Kira ta fada mata su shirya ga magaji Nan ze kaisu Asibitin, Suma zasu samesu a can.. Dakin Zahra zilan ta koma yanda ta barta haka ta sameta, kusa da ita zilan ta matsa tana fadin na hado Miki ko ruwan shayi ne kisha Asibiti zamu". Kai ta girgaiza Mata alamar bazata Sha ba. "Ki daure ko kadan ne Dan Allah Kinga wata Kila ayi Miki allura gara kici ko kadan ne". "Cornflakes". Abinda ta iya fada Kenan ta koma ta kwanta. Ba laifi tasha cornflakes din da Dan dama, rolling kawai tayi suka nufi parlour zilai na rike da ita. Basu jima ba sukaji dirin mota alamar magajin ya karaso Kenan, zilaice ta bude kofar tun Bai karaso ba direct inda zahrar ke kwance ya nufa akan two seater. "Sannu Adda ya jikin naki?" Da kyar ta cira Kai ta dubeshi tana fadin "da sauki". "Allah ya Kara sauki, kamota muje kada Rana ta karayi yanzu twenty five minutes to one fa". Zalai ta riketa tana tafiya da kyar suka fito compound din Zayyan yana zaune Yana game a waya tunda bashi da aikinyi a Nan sai zama,ba zato yaga an fito da Zahra haka, da sauri yayi wurgi da wayar Allah ya taimake kan jacket dinsa ta fada da sai dai wata ba ita ba, ya nufo gurinsu Yana tambayar "Lafiya meya faru? Oga kuwa ya sani? sannu" duk a lokaci daya yake jero wadannan tambayoyin da gani a rude yake. Magaji ne ya nufi inda yake suka Kara gaisawa Yana farin. "Ba wani abun damuwa bane Bata Jin Dadi ne zamuje Asibiti kada ka damu". Zilai magajin ya duba "kun fadawa mujinta kada mu tafi babu sanin sa". "A'a bamu fada Masa ba ai ko daga bayane an fada Masa yanzu dai muje Asibitin wannan ma wani Bata lokacin ne". Da sauri Zayyan ya bude musu gate suka fita yayin da Zayyan din ya dauko wayarsa Yana Kiran Mahmud. Ya kirawo shi Amma Sam taqi shiga sai text kawai Zayyan ya tura Masa ya koma ya zauna yana mamakin ogan nasa na neman gurin Zama a wannan Dan gurin shi ko takura ma yaga alama bayayi wata sabuwar rayuwa yake shimfidawa cikin kwanciyar hankali. Direct A&E magaji ya nufa zilai ce ta taimawa Zahra ta fito daga mota suka shiga ciki shi Kuma magaji ya nufi inda ze karbo file. Ba jimawa yazo ya kawo file din, bayan duguwar tambayar da wata likita da take on call tayi Mata ta rubuta Mata magunguna da allurai da drip ana cikin saka Mata ruwa su Ammah suka shigo dakin, ma'aikatan da masu jiyyar suna ta gaishe da Abba, gaban gadon Abban yaje ya tsaya sunan ta Abban ya Kira ta bude Ido ta kalli Abba tana kokarin tashi zaune "A'a uwata koma ki kwanta ya jikin naki?" "Da sauri Abbana, Ina kwana?" "Lafiya kalau". Ammah ce ta matso tana fadin "sannu Ashe ciwon cikin ne ya tashi?" "Eh Ammah wlh har yafi Wanda nakeyi kamar Zan mutu". Ta fada tana goge hawayen daya zubo Mata. "A'a uwata Banda kuka ai kin girma". Abba ya fada Yana dariya. Itama Zahra dan murmushi tayi ta juya Kai kunya ta kamata ta. Abba Bai bar Asibitin ba Saida aka Maida Zahra Aminity ward. Tun bayan tafiyar su Zahra Zayyan ya kasa tsaye ya kasa zaune, ya nemi number Mahmud tafi cikin carbi amsa daya balarabiyar da akayi linking da computer ke bashi wadda ba fashimta yake ba, sai dai hasashe kawai number Bata tafiya take fada Masa. A gida Abba yayi sallar Azzahar bayan an fito ne ya fadawa Baba malam Zahra tana Asibiti Bata Jin Dadi. Cikin nuna jimami Malam yace "tun yaushe take Asibitin ba'a fada min ba, kuma menene yake damun diyar tawa?". "Wlh ciwon cikin ne take fama dashi tun cikin dare shine dazu Mai Taya ta Zama ta kita Asma'u ta fada mata, sai nasa magaji ya Kai su Asibitin sai suka Bata gado Wai zasuyi Mata hoton cikin da sauran gwaje-gwaje don su fadada bincike akan ciwon tunda ta jima tana fama da lalurar". "Ikon Allah! Allah ya Bata lfy yasa kaffara ne, ai da anyi magana tun a bayan da an Nemo Mata taimakon ciwon Amma yanzu ma Bata baci ba, idan anyi binciken an gano wane irin ciwo ne a fada mini akwai magungunan ciwon cikin Mata da yawa a gurina in sha Allah koda tsiron mahaifa ne da sauransu in Sha Allah zasu narke Koda na aikine zebi jinin al'ada ya narke ya zube". "To in Sha Allah Zan fadawa Asma'u kome Kenan Zan fada maka". Sun jima a harabar gidan Abban kafin suyi sallama. Bayan sallar la'asar malam yasa Habib ya tukashi zuwa Asibitin lokacin da sukaje Zahra tana barci sun gaisa da Ammah Malam ya jajanta Mata Habib ma ya jajanta Mata jikin Zahrar Basu dade ba suka tafi. **** Tun safe da Mahmud ya fita tare da daya daga cikin amuntattun hadimansa na kasar suka fice sun Kai ziyarorin bazata Dan tono wasu laifuka da ake son binnewa, ya dakatar da mutum hudu ya sallami mutane biyu wadanda sukayi sama da fadin maqudan kudade tun bayan rashin sanin inda Mahmud din yake ganin tafiya tayi nisa Kuma baya bibiyar su Sam sai kawai suka tsunduma cikin dukiyar sukayi dumu dumu a ciki, zuwan Sameer ne ya bankado badaqalar wadda tafi karfin shi wadda tasa dole Saida Mai takanas din ya taso, China Kuma issue ne na rufe musu kamfanin laces da materials da akayi Wanda suke zargin ba'a biya kudin harajin kasa ba a tun farkon bude kamfanin, Mahmud yayi kokarin tura duk evidence dinsa ta wibeside nasu Amma sunqi yarda Wanda dole tasa Saida yazo da kansa sannan lamarin ya gyaru. Sai dare sosai ya dawo masaukinsa yaso ya fita ya dan shaqata beach Amma yayi matukar gajiya sosai Koda yayi wanka coffee kawai yayi order da snacks, tunda garin Allah ya waye Bai samu kanshi ba sai yanzu wayarsa ya dauko ya kunna Dan rabon da ya kunna ta tun jiya, sakonni ne suketa shigowa rututu, amma na Zayyan da Habib su sukafi daukar hankalinsa lfy? Ya tambayi kansa. Sakon Zayyan ya fara budewa ai baisan lokacin daya Mike tsaye ba duk gajiyar dake tare dashi Nan take tayi nata guri, cikin tashin hankali ya Fara lalubar number din Zayyan cikin kankanin lokaci Kiran ya shiga, Bai saurari gaisuwar da yake Masa ba ya Fara fad'in "wace irin magana kake min haka? Ashe ajiyekan da nayi bashi da anfani,tun safe Amma kaqi fada min halin da yarinyar mutane take ciki sai yanzu da tsohon Daren nan? Kana son ace ban damu da halinda 'yarsu ke ciki ba tunda throughout yau ban kirata ba nayi busy sosai".."sorry oga wallahi tun lokacin nake neman wayar ka Bata shiga kwata kwata shine nayi make text". "Oh shit! Wlh ban bude wayar ba sai yanzu, yanzu ina zahrar?" "Wallahi Yallabai bansan inda take ba tunda suka fita ban Kara samun wani information akan komai ba". Tsaki Mahmud yayi ya datse kiran. Habib ya lalubo ai sakonma bai tsaya dubawa ba ya Kira shi. "A gaggauce ya amsa sallamar da gaisawar da Habib din yake Masa. "Wai meke fatuwa ne da Zahra?". "Wallahi Nima bani da masaniyar takamaimai kawai dai bayan anyi sallah baba Malam yace na kaishi Asibiti ya gano jikinta sai a lokacin na Sami labarin Bata da lafiya ance ciwon ciki ne, lokacin da mukaje tana barci Amma idan an jima zan koma na qara dubota kome kenan Zan fada maka ka kwantar da hankalinka naji Abban su Yana fadin Daman tana fama dashi ne Saida na yau yafi zafi fiye dana bayan gaskiya Dan har hoto da gwaje-gwaje zasuyi Mata inga in Sha Allah ba wani damuwa kome ake ciki Zan sanar da kai Allah ya Bata lafiya". "Allahumma Amin". Ya fada jikinsa a mace da duk ya shiga cikin damuwa. Number zahrar ya Kira tana ta ringing Amma ba'a dauka ba tsaki yayi tunda yaji haka yasan wayar na gida Basu dauka ba. A karo na farko ya Kira wayar Ammah lokacin wayar na hannun Auta Wanda ya biyo mama da Asabe Asibitin, Dan lokacin da su Ammah suka taho mamar Bata Nan Wai taje duniyar kanwar Babar su Asaben, shine da suka dawo.Abba ke fada Mata Zahra ba lafiya suka taho harda Auta, Autan dake kusa da Mama da wayar Amman a.hannu Yana game na football Mamar dake kusa dashi ta karbi wayar ta mikawa Ammah, batare da Ammah ta duba wayar ba ta daga tana fadin. "Assalamu Alaikum warahamatullahi ta'ala wabarakatuhu". Cikin girmamawa Mahmud ya fara gaishe da Ammah, ita har ga Allah Bata tab'a kawo Mahmud ze Kira ba. Dan Jim yayi Yana Jin nauyin tambayar ta Zahra, Jin shirun yayi yawa bayan gaisuwar yasa Ammar fadin "wa ake nema ne". "Ammah nine na kirane naji ya jikin Fateemah? wlh ban sani ba tun safe ban bude wayar ba muna aiki sai yanzu dana bude ake fada min Bata da lafiya Kuna Asibiti, Dan Allah ayi hakuri in Sha Allah hakan bazata fatuwa ba". Ammah ji tayi kamar ruwa ya cinyeta Ashe sirikinta ne wlh Sam bata Gane shi ba. Ciki Jin kunya da Kara Ammah tace Masa "ba komai ai jikinta da sauki yanzu ma barci takeyi, ya akayi suka fada maka haba ka kwantar da hankalinka Daman takanyi irin wannan ciwon lokaci lokaci sai dai wannan ne ya Dan matsa Mata sukayi admitting din ta zasu bincike a Kai". Ammar ta fada tana dan jin nauyinsa. "To Ammah nagode in Sha Allah da safe Sameer ze shigo zasuje Kano Nan Aminu Kano zasu dubata sosai tunda suna da Gynecologist consultant Ina ga kamar hakan zaifi can suna da kayan aiki na zamani, Zan Kira Abba da Baba Malam muyi maganar, na gode Allah ya Bata lafiya". "Allahumma Amin, Allah ya bada sa'a yayi Albarka". Sukayi sallama. Bayan sunyi sallama Ammah wayar tabi da kallo tana mamakin yanda yake magana da ita tamkar mahaifiyar shi, ya kama sunanta radau. Mama ce ta kalli Ammah tana fad'in "ko mijin nata be? Naji kina masa bayanin yanayin ciwon nata gashi abin takaicin tun ba'aje ko Ina ba ya tsallake ya bar yarinya da wahala, Allah dai yasa ba juduwa yayi ba ya barta da jangwam yanda aka Fara 'yan ciwace ciwacen Nan ai karshen maganar ace ciki ya bayyana shi Kuma yayi masa wuri tunda Daman tsintacciyar magen ce Bata mage ya sulale yabar gari naji ance harda motarta ya tafi Kinga ribar kafa Kenan". Duk surutun da Mama keyi akan Zahra ko kallon ta Ammah batayi ba Dan tasan tana fada ne dan ta Bata Mata Rai kawai, Zilai ma Mai aikin su tana tsaye kusa da Zahra tana gyara Mata hannunta da aka saka mata drip, itama ko tari be kunce Mata ba bata tofa tata ba, to me zata ce maganar ba ta ta bace. Jin ba Wanda ya tofawa Mama ko A a cikin maganarta yasa Asabe cewa. "Wallahi kuwa mama Allah abin tsoro mutum abin tsoro daman nasan in ba wani ikon Allah ba yaron Nan guduwa zeyi yayi gaba kinsan irinsu Yan hujja ne ba wani Zama zeyi na din-din-din ba a garin Nan, abin gudun ma ya jonawa yarinya ala kakai ya tafi ya barta da 'ya'ya, Kuma ki duba kiga yaro Nan a wanke yake Kar bashi da duhun jahilci ko kauyenci ko qanqani haka kawai ya jonawa yarinya alakakai ya gudu ya barta, idan tafiya ta Mike wata Ranar har azo ana yiwa yaro gorin mahaifi ga babu jinjinan dangi kana ji a sheganta yaro ko yarinya". Har Zilai ta baro bakin gadon da zimmar maida martani, sai maganar Zahra suka juyo suka juyo tana kallon Asabe Tana fad'in "lafiya kalau muka rabu, bai Kuma bar garin Nan ba Sai da ya fada min salinsa da iyayensa daga karshe ma mutum ya aje min saboda yana yin rayuwa koda ta Allah ta kasance shine ze kaini har dakin mahaifiyar sa Kinga kuwa ai bani da damuwa a Kan lamarin". ✨✨✨ AUREN HUCE HAUSHI ✨✨✨ MAMAN FATEEMAH. Page 36 ______Zahra tana Gama fadawa Asaben abinda ke cikinta ta juya musu baya, ko banza bazata kwana da fushin zuciya ba, dan tasan idan ba ita tayi magana ba Babu abinda Ammah zata ce Dan sau da yawa idan irin haka ta faru ko kallon Mama batayi sai dai ta bawa banza ajiyarta. Daga Asaben har Mama ba Wanda ya Kara magana,haka Ammar ma da Zilai ba Wanda ko tari ya kuncewa, Auta kuwa wayar mamar ya dauka yaci gaba da sha'aninsa. Shiru dakin ya dauka kamar mutuwa ta ratsa, sallamar Abdul Hakeem da Abba ta katse shirun cikin nuna tsantsar duniyanci Mama ta tashi da sauri tana fadin "Abba har kun karaso sannu da Zuwa" tana gyara Masa kujerar kusa da gadon. Sai da ya zauna sannan ya amsa gaisuwar dasu Zilai da Asabe ke Masa suna jajanta masa, suka gaisa da Abdul Hakeem sannan suka fice daga dakin. Mama ce ta Fara gaishe da Abban kafin Ammah ma ta gaishe shi, sannan Abdul Hakeem ya gaisu dasu Ammar Yana tambayar Mai jikin. Zahar ce ta juyo tana fadin. "Abbana sannu da Zuwa, ina yini?". "Yauwa uwata lafiya kalau Alhamdulillahi jiki yayi kyau". "Eh Abba Daman Kai nake jira kazo kayi musu magana su sallameni mu tafi Nina warke na gaji da Asibitin tunda sunyi min hoton da gwajin da safe mun dawo mu karba bana son kwanan gurin Nan". Ta fada tana hade rai. "Eh Nima abinda ya taso ni Kenan maganar tafiyar taku gidan ne Dan yanzu haka daga office din doctor din muke sun bamu referral Zuwa Aminu Kano kamar yanda mijinki ya bukata yace da safe zaku tafi kiga gynecology doctor ayi bincke tunda ance kin jima kina fama da matsalar". Kafin Ammah tayi magana Mama ta rigata. "Wane irin Kano Kuma ana zaune lafiya, Wai ciwon har ya Kai haka ne idan Asibitin ake son canzawa aje Bauchi Mana Amma har kano akan ciwon mara kawai". Dan murmushi Ammah tayi Bata ce komai ba. Abban ne yace. "Yanzu kina nufin na Kira shi nace masa abinda ya fada baze yuwu ba Kenan ko Kuma Yaya kike son ayi?". Shiru tayi Bata ce komai ba. Ammah ya kalla "kinyi Shiru ko kema hakan ne nufinki". Kai ta girgaiza tana fadin "A'a tunda ga yanda ya fada ai shike da iko da matarsa ita da waye zasu tafi kanon?". "Yace Sameer ne zezo sai zilai ta rakata haka dai ya fada min yanzu da Daren nan" " To Allah ya kaimu yanzu tafiya zamuyi ke Nan?". "Eh haka ne, ku kuje Abdul Hakeem ya mayar daku gida kafin ya dawo ruwan ya Kare sai na raka uwata gida" ya fada Yana murmushi. Sororo Mama tayi Jin Abba da kansa ze maida su Zahra gida. Badai ta tofa ba Amma a ranta taji ba dadi. Tun kafin Ammah ta dauko hand bag dinta Mama ta fice daga dakin. ****** MAHMUD Bayan sun gama waya dasu Abba, Sameer ya Kira harta katse ba'a dauka ba sake Kiran yayi tana Fara ringing ta dauka. "Assalamu Alaikum warahamatullahi ta'ala wabarakatuhu". Ya fada Yana Zama kusa da Fateeha tana shayar da jaririn su. Daga can Mahmud ya amsa sallamar ya Dora da fadin "gobe in Allah ya kaimu ka shiga Azare ka taho da madam zataga doctor a Nan kanon na Kira doctor Haseena za'a kawo patient dina". "Doctor Haseena fa! ita zata duba maka madam din?". "Eh Mana ko da matsala ne?". "A'a gani nayi kada taga anyi Mata cin fuska". "Ba wani damuwa kawai,do what I said". "Ok. In Sha Allah". "Kada ka kaisu gidanka a kaisu gidan dake Nan DAWAKI ROAD su zauna har su Gama abinda zasuyi su koma". "Kana ganin Bai musu girma ba kuwa? dana karkasara aka kaisu yafi kusa da Asibitin ma akan na Nasarawa GRA". "A Nan nake son ta zauna kake maganar girma har wani babban gida ne ka barta ta saba da Zama a irinsu tun yanzu Kai dai kasan kuma abinda zaka fada Mata, a Kai musu duk abinda ya kamata sai dai na fada ba kayi komai kawai, ka fadawa momi ta Basu house maid daya su hadu da tata sai su ringa aikin tare, kayan sakawa dai nasan ba matsala ka Kira Rukayya ta duba abinda ya kamata sai taje ta sawo, ka Bata card din master bedroom na kasa ta sauka a nan. "Shike Nan za'ayi yanda kace, amma baka tunanin taga wata shaida data danganceka a gidan?" "Gaskiya bana tunanin akwai wata alama dake alamtani da gidan". "Anyway, Allah ya kaimu goben, takwaranka na gaisheka". "Oh sorry a shafa kansa sai nazo ganinsa, kaina ne ya dauki zafi". Dan murmushi Sameer ya kashe Kiran Yana kallon Fateeha dake Masa kallon Karin bayani. "Oga ne, Kinga yanda ya shiga damuwa kuwa nifa Banga abinda oga ya damu dashi ba irin yarinyar Nan idan Kika cire Iyayensa to ba na biyunta, ai ban Gama sarewa da lamarin sa ba saida ya nemi guri ya zauna a dakin kofar gida na almajirai duk da gurin bashi da wani aibu". Baki bude Fateeha ta bi Sameer da kallo "dakin Almajirai fa tace shi ogan da kansa? Tab lamarin Azimun ne, Allah ya bamu ko Rabin yanda tayi sa'ar sace zuciyar jarimi kamarsa Wanda Mata ko kallo basu isheshi ba". Lakuce Mata kumatu yayi Yana fadin. "Waya fada miki ba'a Miki so irin Wanda ake mata?" 'yar dariya tayi kawai tasan zance ne inji 'yan magana ******* Lokacin da Ya Abdul Hakeem ya dawo ruwan ya qare har an cire Mata. Cikin marairaita Zahra ta kalli Abban da Ya Abdul Hakeem. "Dan Allah Abba ka tafi Dani gida wlh jiya nasha wahala gashi ba kowa a kusa dani kada na mutu Ni kadai a daki". Saita saka Masa kuka. Baki Ya Abdul Hakeem ya bude alamar mamaki. "Ke! Amma wallahi wannan dai abun kunya ne ki wani kama kuka, kin manta yanzu ba da bane kema fa soon Zaki Zama uwa". "Ungo Abdul uwata kake fadawa haka a gabana? Fita ka Kirawo zulaihatu ta tattara musu magungunan Nan sai mu tafi can din".. Dariya yayi ya fice Yana mamakin Abba yanda yake nunawa Zahra soyayya fiye da kowa. Ba zato ba tsammani Amma taga zilai ta shigo da Kaya a hannu Zahra na biye da ita. "A'a ku kuma ya haka Naga Abba yace ze rakaki gida sai Kuma gaku a nan?" Maganar Abban Ammah taji a bakin kofar parloun. "Ni nace ta taho gida tunda batajin dadi Kuma gida su kadai, gashi Mai gidan nata yace goben zasu wuce kanon gara su kwana a Nan kawai tunda ke dai ba can zaki bita ba gara su tafi a gaban ki". "Ok, ai ban sani ba nayi tunanin ko gaban kanta tayi nasanta da kulafucin gida ganin ta samu dama zata iya fakewa da haka ta taho kaima Abba kasan halinta".. D'an Bata fuska tayi "Kai Ammah Dan Allah fa....." "Kinga uwarta wuce ki kwanta ki huta Keda Baki da lafiya gida dai ai na danki ne, ba Mai hanaki shigowa Zan Kira shi Mahmud din na fada masa ". "To Abba na gode". Ta fada tana shigewa cikin Zilai ta bita da ledar magungunan ta. Abban Bai jima ba ya fice saboda ya baro mutane masu son ganinsa da yawa a kofa. A bakin kofar bedroom din Ammah suka had'u da zilai tana kokarin fitowa. "Ku kuma sai koyo gudun hijira bakwa tsoron maganar mutane masu jiran k'iris su karawa miya gishiri?". "Kayya Ammah idan za'a biyewa maganar mutane ai ko ruwa ruwa ka shiga sunce ka tada k'ura, Kuma ma waye ya ganta Kuma gobe da safe zamu wuce Kano idan Allah ya dawo damu ta wuce dakinta". Zahra na shiga ta fada toilet Dan babu abinda take bukata sama da wanka du ji take jikinta na warin Asaibi. Ta jima tana zubawa kanta ruwa kafin ta fito, sabuwar rigar barci ta dauko cikin kayan Ammah ta saka, ta dauko zumbuelen hijabin Ammah ta Fara sallah. Ammah ce ta shigo dakin lokacin Zahra ta Idar da sallah Tana addu'a, sai da ta shafa sannan ta juyo tana fadin. "Sannu da dawowa Ammah". "A'a ke za'a yiwa sannu, ya jikin naki?". "Da sauki sosai nifa da Abba ze fada Masa bama sai munje wani Kano ba, na warke tunda Daman na Saba duk wata inayi wannan ne kawai ya matsa min sosai". "Kamar Yaya Abba ya fada Masa shi wa za'a fadawa?". Ammah ta fada tana kallon zahrar, Baki ta turo tana fadin. "kema Ammah kin sani fa kowa nake nufi". Dan murmushi tayi kawai. "Ki Kira ki fada Masa bazakije ba Mana sai Abba ne ze Miki tafinta, tunda yace ga yanda yake so ai haka Zaki hakura kuje a duba ki tunda Naga alama Nan din be kwanta Masa ba, Kuma dazu naji kina maidawa Asabe har da Mama magana tona Hana kada na k'ara Jin makamanciyar magana irinta daga bakinki, ki bar mutum da halinsa kedai ki Zama me kauda Kai kawai ki Kuma rike Addu'a takobin mumuni ce kuma hassada ga Mai rabo taki ce". "Kiyi hakuri Ammah in Sha Allah bazan Kara tankawa kowa ba,gani nayi basuji kunyar maganar a gabanki ba shi yasa na rama Nima". Knockig da Sallamar Abdul Hakeem ce ta dakatar da abinda Ammah zata fada. Ammah ce ta amsa sallamar ta bashi uzinin shigowa. Sannu da dare ya Kara yiwa Ammah sannan ya mikawa Zahra wayarsa dake Hannunsa da alama vedio call yakeyi, Yana fadar "gashi Mahmud zeyi magana dake". A d'an kaikaice ta kalli gafen da Ammah take kafin ta Mika hannu ta karbi wayar. Tana karba Ya Abdul Hakeem ya juya, Ammah tabi bayansa tana Masa maganar danyar Madarar da akace ya Aiko da ita da yamma lokacin tana Asibiti. Saida Zahra ta tabbatar sun fice gaba daya daga dakin sannan ta dubi Screen din wayar fuskarsa ta gani Yana kallon ta sai taga yayi wani zuru-zuru kamar Wanda yayi ciwo sai hancinsa ya Kara fitowa zuwat dashi hakensa ma ya qaru. "A hankalin tayi masa sallama tana fadin "Ya M baka da lafiya ne Naga ka rame?". Bushashshen lebensa ya da tura cikin Bakinsa ya lumshe idanunsa tun lokacin da aka fada Masa Bata da lafiya bai samu peace of mind ba sai yanzu daya ganta. Dan ita ke ciwon Amma shi keda zulumin da ramar Dan tun daga lokacin zuwa yanzu daya ganta Baya Jin yaci wani Abu na kirki a cikinsa. A hankali ya bude idonsa ya Dora akan tata fuskar dake kallonsa, wani yarrrr taji da suka hada idon. Cikin tsantsar kasala da jigata ya bude Bakinsa a hankali yace. "My previous hankalina ya tashi, wallahi gani nakeyi kamar Zan rasaki, ya jikin naki? Kuma tun yaushe ciwon ya kamaki Baki fada min ba? sai Zayyan ne yayi min text Wai an wuce dake Asibiti, kinsan kuwa yanda hankalina ya tashi? Daman kina yin irin hakan ne ko yanzu ya Fara Miki?". Dan walainiya tayi da idanunta tana fadin " Naji fa sauki Daman inayi kawai wannan ne yayi min tsanani sosai, amman tunda akayi min allurai da drip na warke, kaga ai ba sai munje Asibtin Malam din ba ko?". Wani kallon Baki da lissafi yayi Mata, shi Yana can ya kasa tsugun da ransa ita Kuma tana fada masa wani shirme. "Zuwa can ba fashi, kuma da izininwa Kika taho gida jinya kin tambayeni Zaki zo gida?" Narai narai tayi da Ido abinda ke tsuma shi kenan yaji Yana neman sakin layi. "Kai Yaya wallahi na fada maka Zanzo gurin Ammah Kuma ka amince kace nazo koka manta Ranar da zaka tafi?" Ta fada a shagwabe tana zubawa Masa sexy eyes dinta da suka Kara wani hasken wahala data Sha. "Kawai dai kin min wayo tunda kin fini sanin takan duniya kin fini ilimin boko me zurfi shine zakiyi min education, haka ake cewa ko?". Shiru tayi Masa. "Kiyi magana Mana nifa bana son Shiru sai Naga kamar jikin ne" "Nifa na fada maka na warke sai wani jikon Kuma". Zaro Ido yayi Yana Mata kallon mamaki. "Sai wani jikon kamar Yaya? Kenan har kina tunanin Zaki qara fuskantar wani ciwon bayan wannan?". Kai ta gyada Masa alamar Eh. "Pls talk ki bude Baki kiyi min bayani as how kike expecting Zaki Kara irin wannan ciwon?". Sai da ta kauda kanta ta daina kallonsa sannan tace Masa. "Nifa each and every month sai nayi wannan ciwon". Ta fada tana Kara juyar da kai. Cikin damuwa yace. "Pls juyo muyi magana Ina son sanin yanda ciwon yake ne Zan fadawa wani doctor Kinga ai saina San komai kafin na fada Masa yanayin ciwon" Cikin Jin kunya da nauyinsa tace. "Nifa idan zanyi period ne nake yin ciwon cikin Baya sauki sai anyi min doclofenic injection yake denawa". "Ok, to idan period din yazo Kuma shike nan baya Kara ciwon?". Kai ta gyada masa. "Ki cire hijabin Naga yanda Kika rame tunda Nima daba ciwon nayi ba na rame lokaci daya dubi yanda nayi Rama? a lokaci aiki ma zanyi amma na kasa tabuka komai". Rufe bakinta tayi cikin mamaki tace. "Dan Allah ka daina haka ka manta a dakin Ammah fa nake idan ta shigo fa ta ganni a yanda nake me kake son na fada Mata?". "To ya za'ayi Kenan Ranar data ganki da ciki Kuma a jikinki tunda kina kunyar taga muna video call ba hijabi kamar Wanda ta aikata alfasha Allah idan na dawo dole asan abinyi na Fara gajiya gaskiya sai ragaita nake kamar marayan da bashi da uwa, alhalin Allah ya Gama min sutura, koba haka ba?". Shiru tayi Kamar ruwa ya cinyeta idan ta biye masa kunya ze Bata tunda taga alama Yana neman fitsare idanunsa. Jin tayi Shiru yasa Shima ya bar zancen ya koma Kan batun tafiyar su Asibiti. "Goben idan Allah ya kaimu magaji ya kaiki ki dauko wayarki tunda tana gida ki dauko Yan abun bukata tunda sai kun Gama komai kafin ku dawo wata Kila zaku dauki lokaci ba'a Gama gwaje-gwajen da zasuyi Miki ba, itama wannan Matar ta dauki abinda ya Kanata nata saiki fada Mata". Sun Dade suna wayar har Ammah ta wuce part din Abba Basu Gama ba, sai kusan Sha daya ya hakura sukayi sallama. Da safe tunda wuri Ammah ta saka magaji yakai Zilai gidan ta karkashe kayan electronics, ta cire duk abinda ake ganin ze iya lalacewa ta Mika gidan maman junior bisa Umarnin Ammah. Karfe bakwai da rabi Mai kyau su zilan sun koma gidan Ammah da kayan Zahra a jaka set biyar da sauran tarkace na bukatar yau da Kullum. Sam Mama Bata da labarin kwanan zahrar a gidan Sai da zilai ta shigo da Kaya a hannu magaji Kuma karamar luggage a hannunsa da sauri ta aje bowl din dake hannunta ta nufo Zilai tana fadin "lafiya kuwa daga Ina haka zilai?" Gaishe ta zilan tayi tana fadin "munje mun daukowa Zahra kayan sawarta tunda Bata koma gidan ba Nan muka kwana daga asibitin gida mukayo". Ikon Allah wallahi ban sani ba, Babu Wanda ya fada min tun daren, Bari na shiga Naga jikin nata". Suka nufi part din Ammah. ✨✨✨ AUREN HUCE HAUSHI ✨✨✨ MAMAN FATEEMAH. Page 37. _______Cikin wani irin takun Jin Dadi da karsashi Mama ta shiga parlourn Ammah tana fadin "Ina patient din take? Ashe nan Kuka kwana jikin ne yaqi Dadi bayan mun taho? wlh ban sani ba sai yanzu da naga zilai ta shigo da kaya ta fada min". Ammah ce ta fito faga kitchen din part din ta tana fafin "ko daya sangarta ce kawai Wai kada ciwon ya tashi cikin dare, kamar an fada Mata a Nan din ciwon baze tashi ba". Dan murmushi Mama tayi "ai kinsan yanda take da son gida ai inaga idan sun dawo ma saita zauna a nan din tunda ba'a San ranar da mijin nata ze dawo ba gara tana kusa tunda Naga alama ba wani iya riqeta zeyi ba da farawa da iyawa, Allah ma yasa Bata da juna biyu ai da abun yayi yawa ga zawarci ga goyo".Dan Jim Ammah tayi Dan da gaske maganar ta doketa wane irin mugun fata ne haka bako kawaici gurin fadin maganar. "Allah ya rufa asiri, duk abinda Allah ya tsarawa zahra Zan karba da hannu biyu ba komai, idan Allah ya hukunta Mata rabuwa dashi bani da tsimi bani da dabara,kinsan shi dare ga Mai rabo hantsi ne, fatan da muke dai Allah ya rabata da wannan ciwon me bibiko". Zahrar ce ta fito Shar da ita cikin doguwar Rigar material Baki da pink din flowers manya ta saka gyale medium a kafadarta tana baza kanshi kamar anyi barin turare a jikinta a hankali ta shigo cikin takunta na rausaya tana amsa wayar sajida wadda ta kirata tana dubata da jiki. "Ke kuma waya fada miki bani da lafiya?" Zahra ta fada tana Zama kusa Auta da yake breakfast ze tafi school. Tunda zahrar ta shigo idanun mama ke bin zahrar da kallo. Wayar taci gaba da amsawa tana fadin "jikin fa da sauki kawai shine yake ta bankama abun kema fa kinsan ciwon tun Mana kazaure shi ne fa yaketa faman tsallen tsinka tsimma akansa". Ta fada tana dariya kasa kasa. "Amma Baki da kirki mijin naki ne me tsallen tsinka tsimman? Saura kadan nayi Miki tawaye bestie irin wannan cin fuska haka?". "Sai anjima Zan kira". Ta fada a hankali duk da Daman idan ba Kuna kusa sisai ba bazakaji abinda take fada ba. Sai da ta kashe wayar sannan da dubi inda Mama take zaune ta Dan rankwafa kada daga zaune tace "Mama Ina kwana?" Ba yabo ba fallasa ta amsa tana fadin "ya jikin duk da dai ba alamar ciwo a tare dake, Banda son yawo Ni banga abin tafiya har Kano ba akan ciwon mara na Mata". Badan Ammah ta jawa Zahra layi ba da Babu abinda ze Hana ta bawa Mama amsar maganarta ba to ba Hali sai zilai ce ta magantu "To Mama tunda yace taje a duba lafiyar ta ai dole taje tunda da gaske Yana cikin damuwa". Dan tabe Baki tayi tana fadin. "Ai kam sai kuje nasan dai rabe-rabe zakuyi a gidan uban gidan nasa". Duk abinda ake Ammah najin su amma ko kallon su batayi ba, haka zilan ma Bata Kara fadin komai ba ta fice daga parlourn. Hamza ne ya leko parlourn ya gaishe da Ammah tunda sun gaisa da Mama, Zahra ta gaishe shi Ya amsa yana fadin "ya jikin naki? Ku fito inji Abba zaku wuce kanon". Ta amsa da "to Yaya, jikin da sauki nafa ware wlh, kawai dai". "To Allah ya Kara lafiya". Ya juya ya koma. Zilai ce ta shigo da sauri tana "Ammah zamu tafi ayi Mana addu'a". Dan murmushi tayi "Allah ya tsare ya bada lafiya". "Allahumma Amin". Gurin Ammah Zahra ta karaso a hankali ta rungumeta kamar zatayi kuka, zamu tafi Ammah saina Kira idan munje kada ki Kira Aunty Hasana tunda Bata Dade da tafiya ba, Allah yasa ma gobe zamu juyo gida wallahi bana son zuwa nifa". Bayan ta Ammah ta Dan shafa tana fadin "kuje ba komai In Sha Allah za'a dace a gano menene matsalar tunda suna da Qualified Gynecologist doctors, Allah ya tsare hanya". Kai ta gyadawa Ammar ta saketa ta koma ta dauki hand bag dinta sai lokacin tayiwa Mama kallon Ido cikin Ido. Zamu tafi Mama sai Allah ya dawo damu". Tayi gaba tana rike da hannun Musaddiq sukayi waje, Bata bi takan abinda mamar ke fada ba, da sauri mamar ta rufa musu baya ko sallama batayiwa Ammah ba, wani lokacin Ammah tana mamakin yanda Mama ke nuna tsana da hassada akan Zahra idan abin ya taso Mata Bata iya hiding dinsa dole saita nuna an gane. "Allah ya raba na gari da mugu li'ilafi quash". Ammar ta fada tana komawa kitchen inda take kokarin hadawa Abba break fast. Zahra na rike da hannun Musaddiq suka fito compound din. Mama na fitowa sukayi kicibus da sahura da sauri ta kyara Mata tabi Zahra a baya, ta nufi part dinta ita Kuma sahurar tabi Zahra da sauri. Ganin Abba a harabar gidan ya hana sahura garasowa gurin zahrar dole taci burki a gefen second gate din. Zahra gurin Abban ta nufa Yana ganota ya Fara fadar "Masha Allah! Uwata jikin yayi kyau, ya kika kwana?". "Da sauki Abba, Ina kwana?" Ta fada tana tsugunnawa kusa dashi. "Lafiya kalau Aina leka dana dawo daga masallaci akace Baki tashi ba". "Eh Ammah ta fada min, nifa Abba dama hakuri akayi da zuwan Nan nafa warke ba inda yake min ciwo yanzu". Sameer ne ya shigo da alama daga wurin Baba Malam yake Dan harda Habib suka shigo, gurin Abba suka nufo Habib ya gaishe da Abban sannan Zahra ta gaishe su shida Sameer din suka dubata, mikewa tayi suka nufi inda Malam Bala direba yake jiran Auta su tafi makaranta, sai ya shiga ya zauna sannan Zahra ta bashi 1k, tace ga kudin chocolate Nan idan ka dawo Ammah zata baka wasu na saka Aunty zulai ta debo maka". "Nagode Aunty Allah ya sauwaqe Miki Zan Miki addu'a idan nayi sallah, malam Bala ne ya karaso suka gaisa da Zahra ya tada motar suka fice Musaddiq Yana daga Mata hannu. Ta juyo kenan ta hango zilai da sahura sun nufi gurin su Abba suna gaishe su sannan Habib ya karbi key din motar suka zuba kayan dake hannun su. Sallama su Sameer sukayiwa Abban suka nufi gurin motar, zahrar ce ta dawo gurin Abban tana fadin "zamu tafi Abbana ayi Mana addu'a" "Allah ya tsare hanya uwata ya Baki lafiya yasa daga wannan zuwa Asibitin a samu warakar wannan ciwon". "Amin Abba nagode mun tafi sai nu dawo" ta juya ta nufi motar. Har gurin motar Abban ya karaso Yana musu Addu'a da fatan sauka lafiya. A hankali Sameer yayi kwana ya nufi gate din fita Abban Yana daga musu hannu, haka ma Ya Hamza shima Saida yaga ficewarsu sannan ya koma side dinsu, sunzo fita Sameer ya dunkulo kudi yaba Mai gadi cikin murna ya Fara jero Masa Addu'oi da fatan Alkhairi har yayi Dan nisa suna jiyo muryarsa. A wurin gidan sarki Habib ya sauka, sukayi sallama da Sameer yayiwa zahra sallama da fatan samun lafiya Mai dorewa, yayi gaba zuwa ina zaya. Sun mika a tafiyar sosai Sameer ya Dan juyo kadan Yana fadin. "Madam tun jiya nake Kiran wayar ki ba'a dauka". Dan kwantar da Kai tayi jikin seat din tana fadin. "Wallahi rabona da wayar tun jiya da safe a gida na barta lokacin Ina Zan iya tunawa da wata waya Ina tunanin ko ranar karshen ce tazo, sai dazu da Aunty zilai ta dauko min nabi wasu missed calls din kafin na Kira taka number din ya Hamza ya shigo yace kazo mu fito, na gode kwarai da kulawar ka Allah ya Raya Mana babyn mu". Ta fada tana Dan murmushi. Shima murmushin yayi tana fadar "wato baby kadai Zaki tambaya Banda mamansa wato saboda sunan mijinki ne son Kai ko?. Hannunta ta saka ta rufe fuskarta. Dariya zilai tayi tana fadin tuba muke Yallabai ai baza'a Fara haka ba, gani tayi baby shine bako". "Kin Kare ta dai kawai Aunty". Tafiyar awa biyu da minti Arba'in da biyar suka shigo Kano. Suna area mariri Sameer ya lalubo Rukayya. "Da fatan komai yayi yanda akeso ya zama ready ko?" Sauraren amsar da take fada Masa yake, kafin yace "ok mun shigo ki Kira mommy tasa salmanu ya kawo iya Rahane yanzu". Bai jira abinda zata fada ba ya kashe Kiran. Wani Kiran ne ya shigo masa, shima dai yana da alaqa da zuwan nasu duk dai zahrar naji tayi mamakin Yanda Sameer yake magana cikin ladabi irin haka to shida waye yake wayar Wanda ya jibinci lamarinta haka? Wata qila inda sukeyiwa aiki ne suka dauki nauyin zawa Asibitin nata, haka ta ringa sakawa da kwancewa, shi Kuma Sameer shiga can kurda can har suka shigo Nasarawa G.R.A sultan road. Tunda suka shigo Kano zilai ke baza idanu, Tana bawa idonta abinci, ita fa zilai duka zuwanta Kano baifi sau uku ba, Shima Ammah take yiwa rakiya idan wani uzurin ze kawota. Gidaje ne na garari take gani da ban mamaki yinsu ake kamar baza'a mutu a barsu ba, tana ganin gidajen da take mu'amala dasu sun Kai sun kawo Amma yanzu sai take ganin tamkar akurki ne kan wadan da take gani Bata gara sarewa ba Saida taga gidan da Sameer ya dosa, take hantar cikinta ta kada, innalilllahi takeyi a zuciyar ta, Nan da nan jibi ya Fara karyo Mata Daman tana mamakin gidan da zahrar ke ciki na can Azaren to kuma saiga wani, duk da Bata San mamallakinsa ba, wata Kila karar kwanace tasa ta biyo zahrar irin wannan gidan da sai ayi dambun Naman ka na waje baiji ba. Kofar wani mahaukacin gate ya tsaya yayi horn sau biyu aka bude suka shige. Ba zilan ba ita kanta Zahra ta sare da lamarin gidan Dan tasan yes Sameer masu kudi ne ko kungiyoyin su suna sakin kudaden aiki kamar ba gobe amma Bata taba tunanin ya mallaki irin wannan mahaukacin gidan ba. Dan da gani ba tambaya mamallakinsa yaci ya tada Kai. A kofar parlourn ginin da yafi ko wane tsaruwa da kyawun gani ya tsaya yana hamdala ga Allah s.w.a. Wata matashiyar buduruwa ce ta fito daga parlourn cikin rigar atamfa fitted tana takun yanga da gayu ta nufo motar tana fadin "sannunku da zuwa, Amma wallahi I am very surprised Dana ganka yanzu". "Rukayya Kenan kin dauka Ina Miki Wasa ne idan Kinga banyi driving ba nine bansa kaina ba". Dariya tayi "ai na yarda Kuma nasan wannan assignment ne me mahimmanci a gurinka". Fitowa yayi Yana fadin "yauwa sannunki da kokari, kuma haka ake tarar Baki a garin ku? kinzo kinata surutu kin tare Mata kofar fita". "Oh! Sorry" ta fada tana budewa Zahra kofa duk da Bata ganinta sosai saboda tintac glass ne a motar. Dan matsawa tayi ta bude Mata kofar, kanshin da yayi Mata sallama ne yaja hankalin Rukayya ta kalli kofar lokacin Zahra ta sako kafarta daya Kan fuskar zahrar idanun Rukayya suka sauka. "Kam bala'i" Rukayyar ta fada a zuciyar ta "wacece wannan din Kuma? Tun jiya lokacin da ya Sameer ya aiketa shopping na abubuwan amfanin gida da kayan Mata ready made take Masa kwawar ya fada Mata na waye? sai dai yace Mata wata ce Zaki ganta yarinya ce ko sa'ar ki Bata kai ba yayanta ne ya hada su ya kawota Asibiti, sai oga yace a sauketa a gidansa har su gama da asibitin. Rasa wane yare Rukayya zatayi Mata tayi saboda tasan wannan ko zo da hausa Bata sani ba duk da shigarta ta hausawa ce. Aunty zulai ce tayi magana lokacin data fito "haba yallabai Ina laifinta gashi ta fito ta tarbe mu". Dan murmushi zahra tayi lokacin data fito daga motar gaba daya ta kalli Rukayyar tana wani smile Mai daukar hankali tana fadin "sannu Aunty mun gode" ta fada tana mika Mata hannu, ba Karamin mamaki Rukayya tayi ba Jin zahrar na zazzaga tsantsar hausa bako gargada. Bangaren Sameer zahrar ta kalla tana fadin "Haba oga Ina laifin Aunty na ko wannan fitowar da tayi ai shima Yana cikin entertaining ne mun gode". Ta fada lokacin data rike hannun Rukayyar. Sai lokacin zilai ta Dan samu Peace of mind ganin Rukayya tasan dai da alama gidan bana macuta bane duk da ba tana zargin Sameer bane,yau din ce wata iri baka saurin amincewa da mutane. "Sannunku da hanya". Rukayyar ta fada tana kallon Zahra, yayin da Sameer ya shiga motar ya nufi parking lot ya ajeta. "Yau Aunty mun gode" Zulai kuwa sai kalle kalle take tana jinjina girman gidan Dan wasu gine - gine take hangowa na Alfarma ga shuke-shuke Nan sai wani sanyin kamshi ke tashi a gidan ko Ina Kuma tas ba alamar datti a cikin, dukiya dai Mai sunan dukiya an kasheta a gidan Nan. Ita tunda uwarta ta kawo ta duniya Bata taba shiga irinsa ba, sai yau da dalilin uwar dakinta Zahra ya kawo ta. Maganar Rukayya ce ta dawo da ita cikin hankalin ta. "Bismillah mu shiga daga ciki". Rukayyar ta fada tana nufar kofar parlourn numbers ta daddanna ta bude musu kofa ita dai zilai yau jinta take kamar ba cikin kasar take ba. Lokacin da suka shiga parlourn ba zilai ba kifin rijiya ita kanta zahrar sai da wani shock ya shigeta na wucin gadi, badan Zahra tana fita waje ba Kuma kakanninta masu dashi ne kuma tayi zaman syprus taga guraren hutawa da yawa da gidajen Alfarma da Babu abinda ze Hana ta zabga kauyanci, dan Babu karya naira tayi kuka a cikin parlourn Nan tamkar fadar sarauniyar ingila komai na ciki off-white ne da sirkin ash colour ba tarkace da yawa sai dai an kawata shi da wasu irin cutains masu azabar kyau dan shi kadai abin kallo ne, sai fremes masu kyau da tsari da wasu irin flowers, sai wani special kamshi daya hadu da sanyin A/C ya bada yanayi Mai dadi, sai plasma kusan bango guda. Zilai dai 'yar kauye sak ta koma ko Zama kasayi tayi sai da Rukayya ta juyo tace Mata Bismillah ki zauna Mana ku Sha ruwa". Ta fada tana yin gaba ta nufi wani steps gurin dining table ta shige wata kwana. Zahra zilai ta kalla "Wai Ina ne Nan din Kuma gidan na wanene nifa duk a rude nake na kasa samun nutsuwa ko kadan, irin wannan gidan ai sai sarki ko wani gagarimin Mai kudi". Da watsa hannu Zahra tayi. "Toni Ina nasan amsar tambayar taki, Nima duk daya muke dake bansan komai ba, nasan dai yace zamu zauna a Nasarawa GRA kawai ba wani Karin bayani da yayi min". Rukayyar ce ta shigo dauke da babban tray da robobin farmfresh dasu ruwa da Shani na gwangwani, sai fruit fresh ones. "Bismillah kusha ruwan sai muje ku huta sai kuci abinci". Sannu Zahra tayi Mata, itama zilan tayi mata, Sameer ne ya shigo da wani matashin saurayi da luggage din Zahra da 'yar madaidaiciyar jakar zilai a hannunsa ya gaishe su ya aje ya koma. Rukayya ce nufo inda Sameer din yake tana fadin "Ya Sameer Dan Allah ka jirani Zan bada sako gurin mommy ka taho min dashi" "Kefa Ruky kina da damuwa kiyi Abu Mai mahimmanci sai ki tsaya kina Wasa". "Allah Yaya da gaske nakeyi ka taimaka min". "Ok" Gurin su Zahra ya duba Yana fadin "sannunku madam kun sha hanya ki huta zuwa dare zamu fita Asibitin doctor tace mu hadu da ita a Nan Asibitin Nasarawa zataga patient yau a can da dare saita dubaki idan yaso sai mu hadu da safe a malam din". "To ba damuwa in Sha Allah Zan shirya da wuri nagode". Ya juya ya fice daga parlourn. Zahra tayi mamakin ganin favourite drinks dinta da aka kawo, more especially farm fresh Amma Bata kawo komai ba ta dauki abin arashi ne kawai. Bayan Sameer Rukayyar tabi suka fice daga parlourn. Saida suka sauka daga steps din gurin sannan Rukayyar ta dubi Sameer tana fadin "big bro Dan Allah wacece wannan din? Meye matsayinta a gurin Ya Mahmud nasan wlh ba banza ba yace a bude Mata wannan apartment din nasa". Tsaki Sameer yayi "na dauka want important Abu Zaki fada min Ashe tsabar gulma ce a cikinki, ba abinda yayi Miki zafi a lamarin yarinyar Nan yanda Kika ganta haka Nima na ganta bansan ko wacece dinsa ba tunda baiso in sani ba, Dan haka kada rawar kanki tasa ki fadawa Dr Haseena wani Abu Koda zata tambayeki kice Baki San komai ba". Tunda ya Fara magana Rukayya tayi zuru tana kallonsa yanda ya kiciccife yasa tayi masa alamar (?) Tasan there's something behind. Amma fadan dayafi karfinka sai ka mayar dashi Wasa. Dan jinjina Kai tayi tana fadin shake Nan Bari na koma kada suga an barsu su kadai". Ta juya ta koma Zuciyar ta fall da tambayoyin da Babu Mai Bata amsarsu. Lokacin da ta shigo sun gama suna Dan hira. Cikin bada uzuri Rukayyar tace "kuyi hakuri na barku ku kadai Bari na Fara rakaki naki masaukin kafin na dawo na rakaki Aunty ta fada tana kallon zulai". "Babu komai muje na shigar Mata da jakar kayanta. Rukayyar ce a gaba su Zahra suna bayanta, saida suka wuce parlour uku kowanne Yana wane na Bata zulai da abin harya daina Bata tsoro tunda taga abin bana karewa bane, wani corridor ta nufa suna biye da ita wasu steps suka gangara suka shiga, wani parlourn suka shiga Mai azabar kyau fiye Dana baya, kofofi biyu ne a cikin wani arc suna kallo juna, kofar hannun dama Rukayyar ta nufa saka Kati ta bude kofar tana tana fadin Bismillah". Tana murmushi. "Mu shiga Mana". Zahra ta fada. "A'a iyakata Nan, dakin na manya ne bani fa hurumin shiga ciki". Jin haka yasa zilai Jan burki, itama jagabar da tasan ciki da Bai na gidan tana fadin haka inaga ita 'yar karere. Aje luggage din tayi tana fadin. "A fito lafiya uwar dakina". Suka juya Rukayyar na fadin Bari muje sai kin fito. "Ok, nagode. Zahrar ta fada tana janye da luggage din ta murda handle din da siririyar sallama a bakinta. Bata iya karawa ba taja ta tsaya tana waro idanu waje na mamakin abinda idonta yayi arba dashi... AUREN HUCE HAUSHi. MAMAN FATEEMAH. Page 38. A hankali ta ringa tafiya kamar wadda ke tsoron kada a kamata, abinda ta gani ne ya Bata matukar mamaki wannan bed room din tamkar an dauko na can Azare na Mahmud an aje a Nan, hatta da curtains din windows din iri daya ne ba banbanci, Abu daya wannan yafi wancen shine girma wannan yafi balance akan wancan, Amma tamkar an dauko shi an aje, ita abin da farko tsoro ya bata hatta kamshin turarensa taji a dakin jiki ba kwari ta dosana ta zauna a gefen bed din tana Kara karewa dakin kallo tabbas a gizo idanunta ke Mata ba abinda ta gani haka yake, bata Kara tabbar da kamshin Mahmud takeji ba Saida ta zauna kamar lokacin ya saka ya fita daga dakin. Dan dam tayi Jin ta Fadi sunan Mahmud fatsal sai taji wani bambarakwai a bakinta duk sai wani irin Abu ya darsu a zuciyar ta. A shagwabe kamar tana magana da wani ta Fara fadin "to me ma zance masa ne? Kuma Wai Nan din dakin waye da suke kamanceceniya da nasa har kanshin ba banbanci?. Ba Mai Bata amsar tambayar Dan haka ta Dan zamo kadan tana janyo luggage dinta tana fito da abinda ke ciki,wanka take sonyi duk jinta take a takure indai tana period sai a hankali sam Bata da sakewa ko misqalazarratin, Banda dole Babu abinda ze sakata barin gida a irin wannan condition din. Luggage dinta ta janyo a hankali ta Fara fito da abinda ke ciki, na Kan mirror ta Fara diba ta nufi inda yake lokacin data karasa ba karamin mamaki tayi ba ganin irin kayan shafar da take amfani dasu har da wasu daga cikin irin turarukanta ta gani Banda su freshner na fesawa. Bata fasa aje na hannunta ba, gurin kayan ta dawo ta bude cloth set din data gani tana budewa tayi arba da kayan Mata Babu abinda Babu, harsu shoes da bags, dasu inner wears. Mayarwa tayi ta rufe ta dawo da kayan a hannu ta mayar inda ta dauko su. Wanka ta shiga Nan ma wata duniya ce aka hada, ta jima tana gasa jikinta Dan idan Tana irin wannan condition din Bata kaunar abinda ze hadata da ruwan sanyi ko kadan. Bata wani Bata lokaci ba gurin shiryawar ta saka doguwar Rigar atamfa glitter purple, Rigar tayi Mata das a jiki mayafi light brown ta saka touching din jikin atamfar sai takalma suma light brown din plat, haka nan taji tana son saka turarensa Mai sanyin kamshin Nan dauka tayi ta fesa ta nufi hanyar ficewa daga dakin. Saida ta fito yanzu ta karewa wannan parlourn kallo yafi duk Wanda ta gani a baya tsaruwa kunjerun dake ciki ko rantsuwa tayi bazatayi kaffara ba Bata taba ganin irinsu ba duk kuwa da gidajen Alfarma data shiga ta bangaren Ummee. A hankali ta ratsa ta wuce tabi hanyar da suka biyo suka shigo. Ba kowa a parlourn lokacin data shiga sai dai tana jiyo Dan Karan plates haka kamar ana wanke-wanke. Zama tayi taga ta inda wani ze gitta tunda ita dai ba sanin Kan gidan tayi ba. Wata Mata taga ta fito daga wajen dining ta wata kofa da manya food warmers a hannunta,ta aje a kan table din har zata juya ko jijinta ne ya Bata da mutum a gurin yasa ta juyo tana duban cikin parlourn, Ido suka hada da Zahra da sauri matar da gangaro daga steps din dining din tana fadin "Masha Allah, ko surukar tamu ce ta fito?". Ta fada tana nufo Zahra dake zauna tana murmushi, itama iya Rahanen murmushi take har ta karaso gurin zahrar. "Sannu Mama Ina yini" Zahrar ta fada. "Yauwa sannu yarinya ya kukazo?" "Lafiya kalau Alhamdulillahi". "To Masha Allah, sunana iya Rahane nice mommy ta turo na zauna dake kafin ki gama abinda ya kawoki". Ta fada tana Dan tsugunnawa a gefen zahrar. "To Mama na gode, Amma Dan Allah ki daina tsuguna mini kinyi jika Dani idan Ni ban Baki irin wannan girman ba to kema bai kamata ki bani ba, Dan Allah ki tashi".. "A'a 'yata Allah ne ya Baki Dan na tsuguna Miki Babu laifi". Kafin zahrar ta samu zarafin Mai da Mata amsa Rukayya ta fito daga inda iya Rahane ta fito ganinta da Zahra yasa Rukayyar ta karaso gurin su tana fadin "har kinyi me?" "Harna fito Ina Zan iya Zama a wancan lungun Ni kadai kamar mayya ai Naga kokarin matar gidan nan data iya zama a cikinsa, Daman jiranki nake dakin da Kika rakani na matar gidan ne gara ki hadani da zilai mu zauna tunda duka kwana nawa zamuyi mu tafi kada a samu matsala kinsan halinmu Mata da zargi naje na manta wani Abu daya danganci namu na Mata a samu rashin yarda a tsakanin masu gidan Dan na bude cloth set Zan zaka kayana saina tarar da kayanta a ciki Kinga ai Bai kamata na shigar Mata dakin ba ya Zama Bata da sirri kenan". "Wannan gaskiya ne ranki shi Dade kinyi tunani me kyau a kam". Iya Rahane ta fada. Zama Rukayyar tayi gefen zahrar tana fadin ai gidan Mai shi ko auren fari baiyi ba, kayan da kika gani duk nakine bana kowa bane Dan ya Sameer ya bani kudi nayo siyayyar jiya Dan a Nan na yini nida su suhaila Dan furnitures din dakin ma jiya aka sakasu Ina ga ba wata macen data taba zama a cikinsa Banda Mai gidan to kece ta biyu da Kika zauna, bama a dakin yace a sauke kiba dayan yace sai Yaya Sameer yace na Baki wannan ya wadatar kawai. "Iya aje a fito da sauran abincin sai muje kiyi lunch din tun, shigarki ciki ya Sameer ke kirana Wai kinci abincin Baki da lafiya na tabbar kin Sha magani ni har mamakinsa nakeyi Bai dauki lamarinki da Wasa ba gaskiya". Iya Rahane ce tace "Haba Rukayya yaushe Alhaji karami Zeyi wasa da lamarin iyalin Mahmud, Nima da Mommy ta kirani Saida ta Kira shi ta fada Masa nice zanzo ya amince kafin Nazo, ya jaddad min na kular Masa da ita yanda ya kamata, Kinga kuwa ai baiyi laifi ba ko?". Kai kawai Rukayyar ta iya gyadawa mamakin duniyar Nan ya gama kasheta a zaune "matar Mahmud? Haba biri yayi Kama da mutum, tasan ba banza ba ya Sameer keta rawar kafa ya kasa tsaye ya kasa zaune akan lamarin, Kuma da alama itama yarinyar ninketa sukayi ta bai-bai Dan da alama batasan waye hakikanin mijin nata ba, gaskiya ta tayata murna dan ta zama Mai sa'a duk da shima Saida ya dauko diamond a cikin zinarai, Dan Daman wannan irin matansu ne. Gurin dining din Rukayya tayi Mata jagora suka nufa tana fadin "kice min matar big bro ce Amma nayi mamaki gaskiya sun lullubeni Amma ki Bari kawai bazance naji ba Naga iya gudun ruwan ya Sameer sai wani cewa yake kanwar abokinsa ce". Ita da zahra Dan murmushi take tunda ba gane Kan zancen tayi ba. Abinci ne yakai kala biyar Rukayya ce ta bubbude wa zahra tana fadin "Auntyn mu ki zabi Wanda kike so a zuba miki". "Kaji Aunty ni basai kin zuba min ba haba dadin sai yayi min yawa hakan ma na gode, ina Aunty zilai tazo muyi lunch din". "A'a nan naki ne ke kadai na Kai Mata nata dakin ta tun dazu". ******** Knocking din kofar akeyi a tana zaune ta Sha uban gayu kamar wadda zata wuri dinner ta biki sai kanshi ke fita a jikinta Mai Dadi tana rike da wayar ta tana addu'oin yaumiyya na cikin du'aul mustajaba. Umarnin shigowa ta bayar tana kallon kofar, Basira ce yarinyar dake aikin shara da goge-goge a bangaren ta, tsugunnawa tayi tana fadin "barka da Asuba Ammi". "Barka kadai Basira har kin fito da wuri haka, lafiya dai ko?" "Lafiya kalau Ammi Daman Hajiya Inna ce tazo ita da Abie". Littafin ta aje akan bed side tana fadin "Hajiya Inna kuma"?" Kai Basira ta gyada alamar eh. "Kije gani Nan fitowa in Sha Allah". Ta nufi clothset dinta ta dauko gyale mahadin shaddar ta fito daga bedroom din. A hankali take saukowa daga stairs din shar da ita tun kafin ta karasa saukowa kamshinta yayi musu sallama, cikin takunta na nutsatstsiyar mace Mai aji da yarda da kanta ta da tarin ilimi Hadi da wayewa, sallama tayi musu tana nufar gurin Hajiya Inna ko inda general yake Bata kalla ba. Kusa da Hajiyar ta zauna lokacin da take amsa sallamar tata. "Ina kwana Hajiya". Cikin nuna kauna da kulawa Hajiyar ta amsa tana tambayar ta Ina su uratu Ammin tace Basu tashi ba tunda yau ba zuwa school. Ammin ta Dan juya bata yarda sun hada Ido dashi ba tace Masa. "Barka da Asuba". Shiru yayi Mata kamar beji abinda ta fada ba, itama Bata kara bi takansa ba, Hajiyar na ankare dasu. Ammin ce tace "Hajiya me yasa Kika fito yanzu da sassafe idan kina son ganina basai ki turo nazo ba basai kin taso da kanki ba Dan Allah kiyi min wannan alfarmar kada wani Abu ya taso nason ganina ki taso ki taho saboda ni". "To in Sha Allah hakan baze Kara fatuwa ba nima ba zuwan kaina bane jiya Muhammadu ya sameni da dare yake fada min wata maganar da banji dadin ta ba, shin da gaske ne bakije inda yake ba tunda Kika dawo? Idan ya Kira wayarki bakya dauka, yazo da kansa yafi sau biyar kin rufe kofa?". Shiru Ammi tayi shi Kuma general kamar ya rungumeta a gaban Hajiyar haka yakeji Dan gani yayi ta wani Kara yin fresh da ita bazaka taba cewa ita ta haifi wadannan yaran ba, ta koma masa danya sharab da ita ga uwa uba ko runhu ka rike Kan sakko bazaka taba ganinta a hargitse ba ta San kanta sosai yanda ya kamata, da kyar ya iya saita kansa a gaban Hajiyar. "Kinyi Shiru zainab kenan abinda ya fada gaskiya ne?" Sadda Kai ta Karayi kasa sai Jin shashshekar ta sukayi. "Subahaballahi haba zainab ko lokacin da lamuran suka jagule Baki zubar da hawaye ba sai yanzu, kiyi hakuri na fada Miki duk Wanda za'ace yayi hakuri to an zalunce shi ki yafewa mijinki wallahi rashin samun kulawar ki tasa ya runtse ido ya iya fada min abinda Bai kamata na sani ba, na roqi arziki ki dubi girman Allah da manzonsa ki rungumi mijinki da 'ya'yan ki kiyi boyayyiyar aure yanda Kika saba". Sai da tayi kukanta Mai isarta sannan ta share hawayen ta sai lokacin taji wani gululo ya fice daga kirjinta. "In Sha Allah ya wuce Hajiya har abada ki tayani bashi hakuri hakan baze qara faruwa ba". Dan karamin tsaki Hajiyar tayi "Babu hakurin da za'a bashi, shida ya shuka rashin kirki, kece dai da hakurin ai cewa nayi bana zuwa shi daya Bata yaje ya gyara kayansa tunda Allah yasa kikazo gidan Nan Baki taba kawo min qararsa ba sai shine gemai gemai dashi ze dauko jiki ya kawo korafi ashe Babu dadi king... Dan gyaran murya yayi "Hajiya kiyi Shiru komai ai ya wuce basai kince komai ba, tunda dai nayi abinda takeso ai shike Nan kowa ya ganni a Nan da ranar Allah na taso tsohuwa ta gaba ta min biko". Ammi dai Shiru tayi Bata tanka ba sai Hajiya Inna ce tayi dan murmushin su na manya Wanda suka San jiya suke ganin yau. Ammi duk sai taji wata kunya ta lullubeta, wani lokacin maza kunyarsu kadan ce wallahi duk girmansu idan sukayi wani abun sai kaji kamar kananun yara, kome ya fadawa Hajiya ya taso ta da wannan safiyar?. "To shike nan sai ka bamu guri ko tunda Allah yasa taga girmana ta yafe". "To shike nan yaushe Zaki koma gida?". Kafin Hajiyar tayi magana Ammi ta rigata. "A Nan zata wuni da magari ba za'a maidata gida". ",To kaji sai ka tafi naka uzurin tunda 'yata ta yanke hukunci". Baice komai ba ya nufi part dinsa da yake bangaren ta, harya danyi nisa ya juyo Yana kallonta ido cikin Ido da wani yanayi a tattare dashi. "Kuyi breakfast Dani a kawo min ciki". Kai ta gyada masa ya wuce ciki. Yi Hajiya Ina tayi kamar bataji me yake fada ba ta cewa Ammi. "Muje ki bude min dakin ko lazimi ban Gama ba yaje ya daukoni Dana ce yaje za'a kawoni ma cewa yayi A'a". Ita dai Ammi ba baka sai kunne tare suka shiga dakin da Hajiyar. ******* A qalla sun dauki minti kusan Sha biyar kafin Zahra ta Gama. Parlour na biyu Rukayyar taja Zahra suka shiga Bai Kai na farkon girma ba Amma ba karya Shima ya hadu kamar jira ake su zauna wayar zahrar ta dauki sansanyan kidan ringtone din ta. "Amma" Ta fada tana picking din Kiran sallamar Ammar ta amsa tana fadin "kiyi hakuri Ammah wallahi yanzu na fito daga wanka naci abinci, yanzu nake son kiranki na fada Miki mun sauka lafiya". Daga can Ammar ta amsa Mata da "babu komai da fatan dai komai lafiya ba wata damuwa? zilai ce taso daga min hankali Wai wani gida aka kawo ku gari guda bata taba shiga ko kwatankwacin irinsa ba kamar Kuna wata kasar ita tsoro takeji". Dariya sosai zahra tayi Jin yanda zilai ta nadi zance ta fesawa Ammah. "Kai haba Ammah kyale Aunty zilai rudunta ne kawai, gidan Dan babba Kam babba ne Amma komai normal Ina Jin gidan wani friend din oga Sameer ne aka kawo mu, Kuma momin su oga Sameer ma Saida ta turo Mai aikinta daya da kanwarsa daya Aunty Rukayya gata ma nuna tare ku gaisa". Wayar zahrar ta mikawa Rukayya suka gaisa da Amma, godiya Ammar ta dinga yiwa Rukayyar har kunya ta kamata tace Kuma ta bawa Zahra number din mommy ta kirata tayi Mata godiya. Sallama sukayi da Ammar suna kashewa Kiran ya shigo international tana gani tasan shine. Dagawa tayi tana masa sallama Jin muryarta ba kamar jiya ba ya sauke ajiyar zuciya a hankali da Bai yarda ba da Sameer ya fada masa kamar batayi ciwo ba sai yanzu da yaji muryarta tana fita ba kamar jiya ba. Sallamar ya amsa Yana fadin "my previous...". Wani deeply saida tsikar jikinta ta bada wani yarrr. "Wash" ta fada. Kara Kiran sunan yayi a hankali ciki wata murya Mai tada zaune tsaye "me ya faru ne to jikin ne"?". "A'a ba komai" ta fada a shagwabe. Rukayya na ganin haka ta Miki tana nuna Mata tana zuwa Dan ta barta ta sake yanda ya kamata. "Alhamdulillahi haka nake son ji, ya ciwon ya daina ko yanayi kadan kadan". "Ya M na warke yanzu ba wani Abu da yake damuna dama mu koma gida kawai tunda ya wuce, kawai naje Naga baby muje mu gaishe da mommy da Umman sajida zuwa jibi mu koma, Dan Allah kace to kaji Kuma fa kaga gidan da oga Sameer ya kawo mu gaskiya ka fada Masa ya mayar damu gidansa ko gidan mommy wallahi yayi girma Ni tsoron inda aka kaini nakeyi gurin yayi nisa da main parlour Kuma wani abin mamaki kasan funitures din dake dakin irin na dakinka ne na Azare komai da komai". Dan Jim yayi kafin yace irin nawa Kuma wace unguwa ya kaiku?". Dan Jim itama tayi. "Ina ga ko Dawako Road Nasarawa G.R.A. "Ok nasan gidan na wani friend dinsa ne, wane bedroom din aka Baki?". " Bangaren dama daga can ciki sosai". Shiru yayi wato Sameer be bude Mata master bedroom din ba kenan. "Precious ki hakura a duba min ke kinsan kuwa tension din dana shiga akan ciwon nan naki? kiyi hakuri ayi bincike akai kawai sai nafi samun kwanciyar hankali, gida Kuma nasan shi Baki da matsala dashi Dan cike yake da tsaro ba wata kafa da za'a shigo cikinsa". "Baka Gane ba nifa ni kadai ce bazan iya kwana a gurin ba sai dai Aunty Rukayya tazo mu kwana". Ta fada kamar zatayi masa kukan shagwaba. "A'a ban Amince ki kwana da kowa ba, ba abinda ze kamaki matsoraciya kawai kice na shirya nida nake fatan Allah ya hore min nayi Miki Wanda yafi wannan girma yanda Zaki sake ki walwala keda yaran mu, to kina tsoron wannan ma inaga Wanda nake fatan ajiye sarauniyar Mata a ciki Zahra fa kike ko cikin taurari keta dabance, haka kawai ki janyo min wata ta hanani rawar gaban hantsi da dare so nake ki ragemin zafi idan da wata a dakin ai kin sabautani ko baza'a taimawa dan malam ba?". Ya fada cikin wata irin kasala wadda ta saka Zahra Jin wani irin Abu a jikinta. "Ya Ilahiy Ajib" Ta fada cikin kasakalliyar murya. "Yan Mata yaya dai Kona gudo ne kina bukatata a kusa" Ya fada Yana huro Mata iskar Bakinsa ta cikin phone din, da sauri ta cire wayar daga kunnanta, Dan da gaske sakon yaje inda aka aike shi kashe Kiran tayi bako sallama. AUREN HUCE HAUSHI. MAMAN FATEEMAH. Page 39. ________Wurin karfe takwas Sameer ya shigo gidan, wayar Rukayya ya Kira yace su fito doctor tana jiransu, lokacin suna bedroom din da zahrar take suna cakusawa da Zahra akan wata Rigar shadda 'yar Mali da Rukayyar ta daukowa Zahra cikin kayan da Sameer ya bada ta sawo haka Nan Rukayyar taga zata Dace da zahrar shi yasa ta nace akan ta sakata ita kuma tana ganin tayi Mata girma da yawa, Jin Kiran Sameer yasa ta hakura ta saka sai gashi tayi Mata das kamar an gwadata aka Dinka. Shar ta fito kamar ka dauke ka buye saboda kyau sai yarintarta ta Kara fitowa, dauri mai kyau Rukayya tayi Mata tunda ta kware har makeup din amare takeyi, light makeup tayi a fuskar ta sai ta fito kamar amarya ranar a yini. "Masha Allah" kadai Rukayya ke fada ba karya kyau daban yake ko ita mace zahra ta tafi da imaninta to yayi namiji Kuma? Bata yarda da kyau idan yayi yawa hadari bane sai yanzu da Zahra ke gaban ta Dan babu namiji da ze ganta Bai Kara kallonta ba. Kasa hakuri Rukayyar tayi Saida ta magantu. "Allah yasa kiyi ta haifowa big bro Yara masu Kama dake gaskiya Ya Mahmud ya Dace ai shi wallahi gaba ta kaishi gara da aka samu wannan incidence din da Bai faru ba yaushe ze gano Mana ke". Ita dai zahra murmushi kawai takeyi, amma Kasan zuciyar ta tambayoyi ne fal, Ta Ina Mahmud ya zama big bro din Rukayya da alama akwai wata dangantaka Mai karfi a tsakanin Sameer dashi bawai aikin NGOs din Nan bane gaskiya. A haka suka fito main parlour suka tarar da Iya Rahane da zilai suna kallon Arewa 24 suna program din mata a yau. "Masha Allah, Allah ya kade mugunji da mugun gani". Iya Rahane ta fada tana kallon Zahra. "Allahumma Amin. Allah ya tsare uwar dakina ya Baki lafiya yasa a dace". Zalai ma ta fada, Rukayya tace "Allahumma Amin, sai mun dawo". Suka nufi hanyar fita, a cikin mota suka iske Sameer, gaba Rukayyar ta shiga ita kuma zahra ta shiga back seat. Basuyi wata tafiya Mai nisa ba suka shiga cikin Asibitin, bayan sun fito daga motar number Dr. Haseenar Sameer ya Kira, saiga wata sub-staff da wayar a hannunta tana fadin "sunnunku da zuwa doctor tace na tafi daku office dinta tana zuwa suna wani aiki ne" "Ok mun gode". Rukayya ta fada. Har cikin office din ta kaisu ta fita Nan Sameer yabar su yace zeje yaga wani friend dinsa Dr. Sulaiman. Bai jima da fita ba aka turo kofar su duka suka juya suna kallon Mai shigowa macece wankan tarwada Mai matsakaicin tsawo fuskarta doguwa ce da maidadaicin idanu da hanci tana sanye da doguwar Rigar material coffee Mai haske tayi rolling da milk din veil fuskarta fal fara'a ta shigo tana fadin " wa nake gani kamar Rukayya a office dina rabon daki tako Nan harna manta Sai dai a waya". Dariya Rukayyar tayi tana fadin "Ina laifin Kiran wayar ma Shima zumunci ne yafi ace ba'ayin ko daya". Direct gurin da suke zaune ta nufa " Kinga kin dauke min hankali Ina ta zuba ban yiwa bakuwa ta sannu da zuwa ba, sorry na barku a zaune ta fada tana kallon zahra" "Lah haba doctor ba komai yanayin aikinku ne hakan". Zama tayi kusa da Rukayya tana maida hankalinta akan Zahra. Patient din dangen ce?" Ta jefawa Rukayya tambayar, da alamun mamaki a fuskar ta. Kai Rukayyar ta gyada mata. "Anyway Bismillah ta fada tana tashi daga gurin ta nufi table dinta. Zahrar ta Mike tabi bayanta. Tambayoyi sosai ta rinqa yiwa zahrar wasu har kunya take kamata ta kasa Bata amsa, tambayar data fi Bata mamaki shine inda take tambayar ta meye tsakanin ta da Mahmud Dange?" Kafin zahrar tayi magana Rukayya ta rigata "sister din abokinsa ce daga Bauchi, kuma matar aure ce Dan naji Baki tambqyeta ba, ita Kuma Bata fada Miki ba". Wata ajiyar zuciya ce ta kubcewa Dr Haseenar har Saida Zahra ta kalleta. "Ai ban sani ba Ruky Naga DANGEN yayi matukar damuwa ne ko yanzu kafin na shigo saida ya kirani yana fada min Kuna Nan Kuna jirana na dubata sosai". Dan smile zahra tayi kawai ita Kuma Rukayya tace "kinsan halinsa baya Wasa da rashin lafiya komai kankantar ta, kinsan suna China Aunty Fateeha ta haihu sending Ya Sameer yayo Nigeria shi ya wuce Dubai". Dan murmushin itama Dr din tayi "zeyi abinda yafi haka in dai Dange ne yanda ya damu Zaki dauka matarsa ce wallahi duk yafa rikice kamar ba dangen da Mata ke fada a kansa ba ko kallo basu isheshi ba Sanda muna school a UK da yawa mutane sunyi mamakin yanda muka Dade dashi ba wani matsalar data faru fatana ya dawo su hadu da Daddy ayi a wuce gurin kawai, kinsan halinsa tunda aka samu matsala Nima fa ta shafeni tunda lokacin da abun ya faru munje gida sokoto shiya Hana ayi abinda za'ayi ta fice yabar kasar Kinga Banda case din Nan ta sister din friend nan tashi Bai Kara kirana ba wlh na tura Masa sako ta email dinsa Amma ba reply". Ita dai zahra ba baka sai kunne wata magana sukeyi wadda ta jefata a kogin tunani akan Mahmud abinda kunnen ta keji daban abinda yake nuna mata daban. "Hum lamarin big bro sai a hankali kin sanshi da zuciya kafin dai yayi fushin ana dadewa Amma idan yayi jam'i yakeyi gurin yanke hukunci sai hakuri komai ze Zama normal". Rukayyar ta fada. Forms ta cikewa Zahra ta test-test Wanda za'ayi Mata ta Mike ta fito daga mazauninta tana fadin kuzo muje ayi wannan testses din Sai Kuma muje ayi scanning mu gani akwai abinda nake tunanin yana kawo matsalar Amma bazamu tambbatar ba sai mun duba. "To Allah yasa a Dace" Rukayya ta fada. Sai da suka Fara zuwa lab sannan suka nufi radiology department inda za'ayi hoton cikin. Dr karima ce tayi mata scanning din tambayoyi ta Riga yiwa Zahrar harta gama. Basu jira karbar result din ba, da safe doctor Haseena zata shiga dasu can Asibitin malam Aminu inda za'a mata saura gwaje-gwajen Nan sun Dan rage ne saboda cunkoson can din. Har gurin mota doctor ta rakasu suna 'yar tsama da Sameer, sannan sukayi sallama Sameer na Mata godiya saboda taki yarda ya biya ko sisi tace patient din DANGE nata ne, itama Zahrar godiya tayi Mata Rukayyar ma haka. Har Sameer yayi ribas doctor Haseena ta daga Masa hannu alamun yazo gyara parking yayi ya fito ya nufo inda take a gefen baranda. "Yana zuwa Bata jira komai ba ta Fara tambayarsa cikin nuna damuwa Dan idanunta har Dan ruwa ya taru a ciki da gani tana cikin damuwa da tashin hankali. " Wannan yarinyar wacece a gurin DANGE?" Iska ya Dan huro daga Bakinsa ya hade hannuwansa a kirji Yana kallonta kawai. "Me yasa Kika yi min wannan tambayar?" "Just pls answer me who's she?" "Abinda ya fada Miki da farko yanzu ma dai shi zan maimaita Miki, kanwar friend dinsa ce daga Bauchi sukazo Kuma matar aure ce abinda na sani kenan". "To Amma me yasa ya shiga damuwa akan lamarin ta ya hanani sakat Ni Kuma nasan wannan ba d'abi'ar DANGE bace". "To ki Kira shi kiji gaskiyar magana daga Bakinsa Mana". Ya fada Yana kokarin barin gurin. "Kada kaji haushina na kasa samun nutsuwa ne" Bai tsaya ba Dan da gaske nema take ta karya Masa gwiwa har yayi abinda baze musu Dadi ba, gara taji daga baya a bakin wani ba shi ba, Daman yasan za'a Rina dole ta kawo wani Abu a ranta yanda ya nuna damuwa akan lamarin Zahrar. Jiki ba kwari ya dawo motar ya tada yabar gurin, har lokacin tana tsaye Bata bar gurin ba. Shi kansa yaji Babu dadi a ransa yanda Haseena ta mace akan Mahmud tun suna UK yasan idan taji yayi aure ba Kara min tashin hankali zata shiga ba. Sai da sukayi nisa da Asibitin sannan Rukayya tayi magana "Dan Allah Yaya kaimu murtala Muhammad way zanyi sayayya a Nameer Sale". Tsaki yayi kadan da gani ranshi ba dadi, "nifa baba son yawo kinga ai saimun koma baya, me yasa Baki fada min ba tun kafin mu fito nasan da zuwan". "Kayi hakuri mantawa nayi Amma muje gobe in Sha Allah naje kawai". Bai Kara kulata ba haka zahra Bata tofa tata ba. Yana zuwa round yayi ya dawo ya nufi murtala Muhammad way din, tare suka shiga da Sameer din yace zahra ta duba abinda take so, har Rukayya ta Gama daukar abinda tazo nema zahra Bata dauki komai ba, ganin haka yasa Rukayyar ta daukar mata kayan shafa dasu turarikan gashi Dana wanka shi Kuma Sameer ya daukar Mata dangin su wafer da ice cream, a hanya hira sosai Rukayya keyi musu Amma ita Zahra hankalinta Yana Kan maganganun doctor ita fa abin yafi karfin tunanin ta ke nan da lauje cikin nadi, shin waye uban gidan wani tsakanin Mahmud da Sameer idan ba kunnenta ne baiyi daidai ba taji Rukayya na cewa Mahmud ya Turio Sameer gida daga China ya wuce Dubai zance yayi dai dai Dana Fateeha matar oga Sameer lokaci tafiyar su. Har suka shigo unguwar hankalin ta baya tare da ita tayi zurfi cikin tunanin makomarta kodai yanda ya taba fada Mata Yana yaudarar matan ne ya gudu dasu tunda yanzu yasa an dauko su ba Wanda yasan inda ya kawo su daga Rukayyar har Sameer din ba Wanda yasan takamaimai Ina ne asalinsu an kawo su ita da baiwar Allah an killace su a wannan uban gidan kamar resident na matar shugaban kasa. Sai da Rukayya ta Dan tabata lokacin da suka tsaya a kofar parlourn Dan da gaske tayi mugun zurfi a tunanin Dan zabura tana Fadi. "wallahi har naji tsoro". "Ai ke dince Ina ta magana Amma kinyi Zurfi a cikin tunanin, ki rage yawan tunani saboda lafiyarki kinsa Yana shafar lafiyyar Dan Adam". "In Sha Allah Zan Dena na gode". Ta yungura ta fito Bata jira ba ta nufi kofar shiga tana fadin oga Sameer sai da safe kaina yake Dan Sara min a shafa min Kan Abeed" Dariya Sameer. "Zeji in Sha Allah Banda mamansa ko?" "Kaina bisa wuyana na Isa ayi min gaisuwa, zanzo muyi jegon tare". Wani kallo Rukayya tayi Mata tayi wani killer smile ta matso daidai kunnen ta "saurin me kikeyi in dai jego ne kamar yaune kinsan Yayana ba rago bane daina gaigaye zakiçi tumo". Tayi gaba abinta kamar Bata Fadi komai ba. Ido Zahra ta zaro tabi bayanta da kallo, ta fuske kamar ba ita ta Fadi maganar ba. Ganin haka yasa Sameer ma ya basar ya dauko wasu ledojin yabi bayan Rukayya data dauko wasu. A Nan parlour sukayi sallama da Sameer ya tafi, su zilan Basu tashi daga kallon ba suka Yi musu sannu da zuwa tare Da tambayar ya jikin nata, bata jima ba ta dauki kedar cosmetic din da robar ice cream Daya da biscuits da chocolates ta nufi hanyar masaukinta tunda yace Mata ba komai a gidan da tsaro sosai ta Sami kwari gwiwa da kwanciyar hankali, tana barin gurin ta dauko wayarta ta kasheta gaba daya tana fadin. Wallahi kwana kusa ba zasu gaisa ba tunda shi wani irin mutum ne marar Alqibla. Kuma tafiyar ta zatayi ta koma inda ta fito haka kawai Kullum ita kenan cikin matsala gara ta koyi jajurcewa itama kowa ya samu dama saiya ringa dokata kamar wata ball impossible wallahi". Ta fada tana zura katin bude kofar ta shige ciki, a Kan sofa ta zube kayan ta shiga cire kayan jikinta Daman duk sun dameta, wanka ta shiga Dan wallahi barci takeji, barcinta zatayi tasan mutum Bata wuce kaddararsa. ****** A gajiye ya shigo masaukinsa yau throughout bai samu hutu ba, hankalinsa gaba Daya yayi gida so yake ya ganta ra'ayal ain bawai ta wayar ba yaji dumin jikinta ya tarairaiyi kayarsa suyi barci tare su tashi tare ya gaji da watangaririyar Nan gara ayi wadda za'ayi kawai game din ya Zama over. Saida yayi wanka yayi order coffee sannan ya janyo wayar ya shiga nemanta da gaske yayi kewarta ba kadan ba, shifa yana ganin yarinyar Nan itace weakness dinsa duk inda take tana manne a kirjinsa ko barci yake itace a cikin barcin idan ba ganinta yayi ba ko yaji muryar da da akwai damuw, yaga alama any nan gaba ze iya kulla wani abun arziki kuwa? tun yanzu da gishiri bai Sha Kan kazar ba yana jinsa haka Yaya idan labarin ya sauya salo? Abin mamaki wayar switch off. Zuru yayi Yana kallon wayar "me kenan?" Yasan dai ba matsalar charge bane, Sameer ya Kira, duk da basu Dade da Gama waya ba. Sameer yayi mamakin ganin wani Kiran nasa. Kafin Sameer ya Kai ga magana Mahmud ya Riga shi. "Meya faru ne a Asibitin naji wayarta a rufe ko jikin ne ta tashi da akayi Mata gwaje-gwajen?" "A'a gaskiya normal muka dawo har muka biya nan Murtala Muhammad way sukayi sayayya Kasan Rukayya bataso a zauna lafiya,idan tajita da kudi ba zaman lafiya. Dan Allah ka daina turo mata kudi har madam tabar garin nan, kasan Ruky da yawo Kullum aka fita saita qirqiro zuwa wani gurin, wani Abun ne ya faru yanzun ?" "A'a ba komai, kada ka manta da maganar kayan da za'a sauke gobe a Nan kanon a turasu can Azaren munyi magana da Habib dazu". "Ok in Sha Allah". Sukayi sallama, ji yayi baze iya fada masa komai ba. Wayar ya aje kusa dashi wani tunani yayi sai yaji dariya ta kubce masa "zakiyi bayani da yaren garinku yarinya duk yanda akayi taji wata maganar yanzu a Asibitin yasan Haseena farin sani yanda yaji ta damu da sanin relationship din dake tsakanin sa da zahra yasan zatayi duk yanda zatayi ta shigo da wata maganar wadda zatayi touching dinta tunda shekarun da wayonsu ba Daya bane. Itama Zahra kasa cin komai tayi fridge ta bude ta saka ice cream din da chocolates tayi kwanciyar ta bayan tayi Addu'a, amma barcin Kuma yace baisan zancen ba, tashi tayi zaune a tsakiyar gadon tana tariyo rayuwarta ta baya "ko yaushe Zan Zama stable a rayuwata? sai hawaye suka zubo Mata "Ubangji ka hanani ganin bakin cikin gidan Aure, lamarin Yana neman yafi karfina ka jibinci lamurana Dan isar fiyayyan halitta Annabin Rahama Muhammad s a w.w. Bansan ko waye ba wannan bawan naka, kafini saninsa ka amintar Dani a cikin lamarinsa daka barni na tozarta, ka kareni daga dariyar makiyana Ubangiji kasan ko suwaye suke mini yankan Bata a cikin lamarina, kayi min kariya ka bani juriyar abinda ka jarrabeni dashi kasa ya zamar min kaffara. Tasa tafin hannunta a fuskarta taAUREN HUCE HAUSHI. MAMAN FATEEMAH. Page 40. ______ karfe takwas saura Zahra ta fito cikin shigarsu ta asali doguwar Riga baka Mai aikin zare maroon sai kananan stones har kasa,tayi rolling da maroon din veil, cikin takunta na rausaya take gannaro steps din, tana baza sansanyan kamshi, ba kowa a parlourn sai wani sanyi da kamshin freshners ke tashi, Dan Jim tayi tana tunanin ta koma kota zauna sai Kuma ta jiyo alamun motsin kwanuka a kitchen gurin da taga suna shiga ta nufa tunda ba sanin Kan gidan tayi ba, tunda ta shigo iyakarta Nan sai Kuma bedroom din da take, tana dosar gurin wani kamshin girki yayi Mata sallama, babban kitchen ne na zamani Mai kunshe da na'urori birjik kamar a wani babban Hotel ko irin modern restaurant din nan iya Rahane ta gani tana yanka wani Abu yayin da zilai ke tsaye tana duba wani abu a tukunya. Sallama tayi musu tana fadin "Ina kwanan ku". A tare suka juyo suna amsawa tare da fadin "ya Kika kwana da jikin?". Dan juya Kai tayi tana fadin. "Nifa Babu abinda ke damuna kawai dai Dan a dunga yawo ne da Bata lokaci, wallahi har kunya nake ji" . "A kul Kika Kara fadar haka tunda mijinki yace Kizo a duba aga menene matsalarki kada ki watsa Masa qasa a Ido ki sage Masa gwiwa akan kokarinsa, kije idan Allah yasa Babu komai shike Nan idan Kuma anga abinda ke kawo ciwon a magance shi". "Wannan gaskiya ne". Zilai ta fada tana sauke girkin. "To in Sha Allah na daina iya". "Yauwa kokefa fa ai idan Kika Fara da haka ko lalular da tafi haka baze Maida hankalinsa ba duk da ba fata ake ba". "Dan Allah Aunty zilai bani wayarki na Kira Ammah tawa tun jiya ta kashe kanta taki kunnuwa". Ta fada tana istigifari a zuciyar ta Dan tasan karya ta shara. " To Bari na dauko Miki tana can a daki" Ta wanke hannunta ta nufi kafar fita Zahrar tana biye da ita, sai da suka fito zilan ta kalli Zahra "uwar dakina Dan Allah Wai Kinga kuwa dakin da aka ajeni a ciki Dan Allah muje kiga wannan duniyar da aka sakani kamar dakin gidanki,to acan dai bana Hawa gadon Amma wannan akai na kwana har naso in makara Allah yasa ita Iya Rahane Bata makara ba". Dariya Zahra tayi tana fadin "daina fada Aunty zilai sai a Raina mu wallahi, muje Naga dakin naki Daman ban San inda kike ba Koda tsoro ze kamani sai nayo gudun hijira". A parlour na biyu suka shiga wani corridor bazaka taba cewa da dakuna a gurin ba steps ne kamar goma suka haura sama Nan ma wani parlourn ne da two three bedrooms biyu suna kallon juna sai Daya daga gefe. "Masha Allah" Zahra ke fada a zuciyar ta tana mamakin gidan Wai wane irin gida ne wannan gari guda compartment guda kawai ya hada irin wadannan mahaukatan falukan da bedrooms din Nan to yaya sauran parts din suke?. Dakin dake hannun hagu ta nufa ta bude, daga inda Zahra take ta hango wani Royal bed milk Mai azabar kyau, Bata Kara gaskata maganar zilan ba Saida ta shiga ciki, a gefen bed din Zahra ta zauna tana fadin "Bari na Dana gadon Aunty zilai". Dariya sukayi su suka "kin gani ko wallahi nifa a jiya da kyar nayi barci duk zulumi ya isheni ji nayi Ina tsoron gidan yayi girma da yawa, na jinjinawa matar gidan". "Wai Mai gidan Bai taba aure ba a gaba dai ze kawo matar". Baki zilai ta Kama tana fadin "to shi wane irin kudi ke gareshi da ze Gina irin wannan gidan Yana saurayinsa". "Bani wayar Aunty zilai wannan hirar ba karewa zatayi ba kada lokaci ya kure yau daga Asibitin cikin gari zamu gidan su oga Sameer na gaishe da mommy". Wayar ta Bata suka fito tare ta Kira Ammah suka gaisa sun jima tana fada Mata abubuwan da akayi mata jiya da Kuma komawar da zasuyi yau, karfafa Mata gwiwa itama Ammar tayi tana fada mata ta kwantar da hankalinta In Sha Allah ba komai. Lokacin da suka fito har Iya Rahane ta shirya table din Rukayya ma ta fito. Kallon su Rukayyar takeyi ganin daga bangaren da suka fito. "Aunty Rukayya Ina kwana?" Zahra ta fada. ",Lafiya kalau matar big bro, ya Naga kin fito daga bangaren mu". "Au kema a can Kika zauna kika ki zama a dayan dakin kusa Dani". Baki ta bade tana kallon Zahra. "Na shiga dakin Mai gidan na zauna tab ai wannan part din sai ku". "Mu suwa daga zuwa bakunta sai mu zaqe Ina laifin can din wallahi transfer zanyi, Ina dalili Ni kadai kamar mayya kufa Nan ku uku ko ihun neman taimako kayi an taimaka maka amman Ni kuwa ko kasheni za'ayi sai dai a dauki gawar da safe". "Tab wallahi ba inda Zaki zauna a Nan ba haka big bro yace ba,a can yace ki zauna Dan haka Babu Mai canza wannan Umarnin". Dan turo Baki tayi "Ni na taba ganin haka mutum ya ringa saka doka a gidan mutane inaga baisan girman gidan ba shi yasa yake bada wannan Umarnin, gaskiya da sake". Time Rukayya ta duba a waya kizo muyi break yanzu zakiga ya Sameer yazo tunda da wuri za'ayi Miki sauran gwajin". Suna cikin break din Sameer yazo Saida ya jira a mota suka Gama sannan suka tafi, a ANC department suka samu doctor Haseenar sun awon ciki. Ba yabo ba fallasa ta tarbesu ba kamar jiya ba ko yanda suka ringa Yi jiya da Rukayya yau ba haka bane daga gaisawa Bata Kara cewa komai ba, itama Zahra saita Kama kanta Rukayyar ma haka. Gwajin jini ta Kara tura Zahrar ta hadasu da wata ma'aikaciyar su ta rakasu main lab aka dauki jinin. Lokacin da suka dawo sun Gama ante-natal din gwajin jira ta dauko da scanning din ta Kira Sameer tana fadin mu hadu a office dina". Ta kashe tana fadin Bismillah Ruky muje office dina tunda mun Gama da Ante-natal sai zuwa anjima zamu Fara gyne". A kofar office din suka samu Sameer din ya rigasu zuwa. Sai da suka zauna sannan suka gaisa da Sameer din, bayani ta farayi Masa na gwaje-gwajen jinin jiya "a cikin jininta ba wata cuta ko kadan kawai scanning ne ya nuna Mana akwai matsala a mahaifarta ta fibroid amman be wani girma sosai ba za'ayi aiki a cire mata tun kafin ya girma Amma zamuyi admitting dinta zuwa one week tana karbar magani kafin ayi surgery din, Dan haka sai ta Kira mijinta ta fada masa yazo da mutane muna son jini leda biyu, zamu jira results din Nan ya fito total blood count za'ayi Mata". Rukayya ce tayi farat ta tambayi doctor Haseenar "yanzu dole sai tiyata baza'a iya Shan magani ba a warke?" Kallon tsab Dr Haseenar tayi Mata kafin tace "hanya mafi saukin rabuwa dashi ta sai dai aikin gaskiya". Tunda doctor Haseena ta Fara bayani gaban Zahra ya yanke ya Fadi idan da abinda taki jini a rayuwar duniyar Nan to tiyata ce. Nisawa Sameer yayi kafin ya samu karfin halin fadin. "Thank you so much doctor kome kenan zakiji idan munyi communicating da mijinta saina kiraki later" "Ok.ba damuwa Allah ya sauwaqe". "Amin". Rukayya ta fada Dan zahra ba bakin magana har suka shiga mota tana cikin tashin hankali, kuka takeyi irin na zuci din Nan sai dai hawaye kamar an bude famfo. Saida suka fita daga Asibitin har sun shiga court road sannan Sameer ya Dan juyo, Madam kiyi hakuri in Sha Allah ba wata matsala idan Allah yasa yin surgery din ne yafi Alkhairi ayi kawai Kinga kema saiki huta da zulumin ciwo duk wata". Rukayya ce juyo tana fadin "gaskiya kada ki yarda a yanka ki haka kawai Ni banma yarda da maganar Haseena ba, kawai ta jawo Miki wahala Ni Daman da anyi shawara Dani da Babu abinda zesa Haseena ta duba matar big bro haka kawai taje ta jawo Mata matsala da gangan bakaga yau sai wani share mutane takeyi ba, wani ya Hana big bro din ya aure ta". Wata uwar harara Sameer ya zubawa Rukayya "Billahillazi Zan saukeki a Nan ke wace irin mutumce da bakinki bashi da controlto me kikayi ke Nan? wannan ai shashanci ne keda Zaki kwantar Mata da hankalinta shine Kika sokawa zancen wuqa". Ita dai Zahra maganganun Rukayya sun daga Mata hankalin kenan da wata jikakkiya a tsakanin wannan likitar da Mahmud. Wallahi ko likitoci sun Kare wannan ba zata Kara dubata ba shi yasa Kennan jiya ta damu da sanin waye mijinta da dangartakar ta da Mahmud. Tunda Sameer ya yiwa Rukayya buyagi Bata kara magana ba har sukazo junction din gidan shatima. "Wai yaushe mommy taje gidan Hajyr makwararin?". "Dazu da safe na kaita Wai zasu karbi lefen mujahida". "Ok Allah ya Sanya Alkhairi. Dan Allah ya Sameer Zan sayi alawar Madara idan ka tsallaka Zan kaiwa Hajiyar makwarari". "Kice dai Zaki saya bawai Zaki sayawa Hajiyar makwararin ba". "Allah tana son shi sosai" A kofar gidan Hajiyar yayi parking Babar mommy ce. Da karadi Rukayya ta shigo gida yayin da Zahra da Sameerke biye da ita a baya, suna runfa ana hira da kunnen Rukayya da 'ya'yan dangi da mommy masu karbar lefen basu Fara zuwa ba gaishe dasu yaran sukayi suka fice, sukabar mommy kawai. Cikin nuna kulawar mommy ta kalli Rukayya dake gaba. "Ba dai har kun gama da asibitin ba?" " Mun Gama kin ganta Nan Wai doctor Haseena tace zata yankata tayi Mata tiyata Dan nace ban yarda da ita ba shine ya Sameer yake ganin bekena". Sallama Zahra tayi tana Dan tsugunnawa tana gaishe da mommy cikin muryarta Mai sanyi da nutsuwa da Kuma alamun tasha kuka. Mommy kallonta tayi tana fadin "Masha Allah tabarakalla sannu ya jikin naki?" Da sauki sosai". To Allah ya Kara lafiya naji Rukayyar na fadin tiyata za'ayi Miki". "Eh haka suka fada" Hajiyar makwararin ce ta fito tana fadin "wa nakeji kamar Rakiya a gidan nan waye ba lafiya naji ana magana tiyata". " Kin ganta Hajiya, matar Mahmud mutumin ki ce". Mommy ta nuna zahra. " Wai Amaryar ce? Sannu kinji menene ya sameki?" Rukayya ce ta fada Mata. Mommy ta kalla "Ni Zan hada Mata maganin wannan lalurar ba sai anyi Mata aiki ba, ki huta Rukayya ki shiga Nan kurmi ki sawo min abin hada maganin a Nan na hada Mata insha Allah sai dai ya narke yabi jinin al'ada. "Amma gaskiya ba wanda ze yanka ta Kamar kabewa ku 'ya'yan zamani komai a yanka ta haka ne daji yake shiga ai ta fama da rai idan yazo da karar kwana kiga an mutu, daina kuka, samiru kiwawo min mijin nata na fada Masa da bakina Babu me yi Mata danyan aiki ko haihuwar fari Bata yi ba a jawo mata tsuguniya mazan yanzu marasa hakuri". Ta fada tana nufar uwar dakanta. Ita dai mommy Shiru tayi Saida Hajiyar ta shige sannan ta dubi Rukayya "Wai Ke Sai yaushe hankali ze Gama Miki jiki? Kinzo kin kwatsa zance gashi Nan kin tubzura Hajiya Mai hanata hada maganin Nan sai Allah, itama Kuma Mai lalurar maimakon ki kwantar mata da hankalinta A'a tashin farko kin sokawa zancen wuka, ai kin kyauta". "Wallahi ba haka bane mommy Kinga dai muna good term da Haseena amma wallahi yau kamar ma Bata taba gani na ba sai cin magani take yiwa mutane da dacin rai want ya Hana Ya Mahmud din ya aureta taga yarinya ta gigice zatayi mata illa haka kawai". Maficin dake kusa da ita Mommy ta jefawa Rukayya tana fadin fita ki bani guri tunda kin Zama babbar kwabo kin tasa yarinya gaba kina fadar abinda be Dace ba". Wata uwar harara Sameer ya saukewa Ruky ji yake kamar yayi Mata duka duk ta cakude lamarin tana kokarin ta saka jinin yarinyar mutane ya hau, tun sassafe Mahmud ya Kira shi Yana fada Masa ya kira Rukayya yace ta fadawa Zahra ta bude wayarta ya manta shaf sai fa yanzu ya tuna. Wayarsa ce ta Fara ringing "shine ya kira" ya fadawa mommy. "Ka dauka kayi Masa bayanin halin da ake ciki". "Nasan Haseena ce ta fada Masa shine ya Kira yaji". Wayar ya saka a speaker yanda zahrar ma zataji. Bai jira komai ba ya Fara fadin "Sameer wace magana naji Haseena tana fada min? kada ka Bari su taba min yarinyar nan Zan kaita inda ya Dace, naji tana fada min wasu nonsense wallahi idan na shigo saina Bata Mata rai, ita harta isa ta fada min son ranta who is she? Yanzu ina ita zahran take? Tun jiya jikina ya bani an samu problem wayar ta fa ta rufe ta Hana nayi magana da ita fa". Tashi Sameer yayi tsam ya fita ya cire wayar daga speaker saboda kada yayi katobara. "Gamu Nan a makwarari gidan Hajiya Zahrar sai kuka takeyi,ita Kuma Ruky sai tinzira ta take kada ta Bari a yankata har Hajiyar makwarari taji tayi tsallen Albarka tace bata san wannan magana ba, ita zata hada Mata maganin hausa Wanda ze narke ciwon, wallahi sun caza min kai har na rasa yanda zanyi da rigimar Hajiyar, yanzu haka kasuwar kurmi zata aiki Rukayya ta sawo Mata mahadin maganin da zata hadawa zahrar". "Yanzu dai bazan Gane kome kake fada ba hadani da Zahrar muyi magana" "Ok Bari na kira ta dakin mujahida Naga ba kowa a ciki ka kwantar Mata da hankali duk ta shiga damuwa sosai sai kuka takeyi" Rukayya dake zaune a tsakar gida ya yiwa nuni data Kira Zahra, lokacin da suka fito Yana tsaye suna ciga da maganar. Wayar ya Miko Mata ya nuna Mata dakin mujahida yayi nufi waje. Tana shiga cikin dakin tana Jinsa Yana faman hello, hello tayi shiru karshe ma ta sakata wayar a flight mood tayi kwanciyarta a katifar mujahadar tana goge hawaye. "Me kake son fada min Kuma? naji komai me Za'ayi bazan zauna a garin Nan ba wallahi, gida Zan tafi kuma idan ma ciwon ne ai Ina da inda za'ayi min maganin ba sai Nan ba, da gata na da komai na zauna sai watangaririya nake yi Dani".AUREN HUCE HAUSHI. MAMAN FATEEMAH. Page 41. 📖🖋️ ________Wani irin barci me nauyi yayi awon gaba da zahra, sai da Sameer ya shigo yace Rukayya ta duba Masa Zahra oga ya Kira yace Masa da matsala. Dakin Rukayya ta shiga ganin Zahrar tana barci ga wayar Ya Sameer a gefen ta, daukar wayar tayi tana dubawa a airplane mode taga wayar 'yar dariya tayi tana fadin "good yarinya kinsan kanki kenan ai Ina bayanki ki tsaya tsayin daka akan wannan mijin naki idanun Mata a kansa suke kinyi dai-dai wallahi". Wayar ta cire daga flight mode din tayi waje da sauri tana fadin "gashi ya Sameer wallahi barci takeyi" . Wayar ya Karba Yana dubawa gashi Nan a kunne take haka datar itama ba wani matsala. Tsaki yayi kadan Yana fadin "duk nema suke su dagulamin lissafi wallahi har na rasa Yanda zanyi" . Rukayya najinsa tayi Shiru haushinsa takeji tun buyagin da ya yi Mata dazu,waje ya juya ya fita Yana kokarin Kiran waya. Hajiyar makwarari ce ta fito daga daki da manyan tabarmin roba a hannu tana fadin "zo Nan Rakiya ki shimfida su cikin baranda kafin mutane su Fara taruwa". Zuburo Baki tayi "Allah ki daina fada min sunan nan ni sunana Rukayya haka a ringa batawa mutum suna". Ta taso tana karbar tabarmin. "Gidanku, nace Rakiya ba sunan ki bane, Kizo ki shiga kurmin ki karbo min masoro gurin Alhajin Baba nayi na hadawa yarinyar Nan magani na Bata tun yau ta Fara amfani dashi ba'a bori da sanyin jiki". Saida ta Gama shimfidar ta shiga gurin Hajiyar cikin falonta suna duba kayan da za'a bawa masu kawo kefen robar da aka zuba chicken pepper ta bude tana fadin "bari na dauki Daya naji kamshin yayi min Dadi". "Ki rufe wannan gashi can a kitchen a waje ki diba harda snacks din duka, Amma ki Fara karbo Mata sakon a kasuwar tukunna kuje da sadiya ta rakaki ku shiga a dai daita tunda ba nisa ga cunkoson cikin kasuwa Kuma kinsan Sameer baze Baki motarsa ba, wadda mukazo da ita Kuma Aliyu yayi nasa gurin da ita". Basu dauki minti talatin ba suka dawo da sakon har lokacin Zahra barci take sai da jama'a sun Fara taruwa a gidan duk dangi need sai dai-daikun Yan uwan mahaifar mujahidar. A blender hajiyar taba mommy ta nika Mata masoron ta juyo mata shi a cikin robar da Hajiyar ta bada a zuba a ciki. Lokacin da mommy ta kawo Mata Hajiyar da kanta ta nufi dakin mujahidar tana fadin "Ina matar Mahmudun take?. Barcinta take sadidan Dan tabata Hajiyar tayi tana fadin. "Tashi 'yar nan ga maganin lalurar ki da izinin Allah". Tashi zahrar tayi tana bin Hajiyar da kallo lokacin data aje robar kusa da ita. "Bude ki gani sai nayi Miki bayanin yanda za'ayi dashi". Batayi musu ba ta bude robar taga garin masoron. "Kina jina? Abinda za'ayi dashi ki ringa diba Kashi Daya bisa hudu na karamin cokalin shayi kina zubawa a ruwab zafi tafasashshe cikin kofin ok ki barshi yayi minti ashirin a ciki sai ki tace ki Shanye ruwan,haka Zaki ringa yi har ya Kare in Sha Allah ze narke yabi jinin al'adarki ya fice, ki rabu da wannan shirmen komai ace za'a yanka mutum kamar kabewa" 'yar dariya Zahra tayi tana fadin in Sha Allah zanyi na gode madallah Allah ya saka da Alkhairi". "Allahumma Amin. Allah ya Baki lafiya,ayi ta hakuri irin mijinki Mata Ido rufe suke nemansu sai kin kauda Kai zakiçi ribar zaman aurenki. Amma kada ki kuskura ki yarda a nuna Miki San iyawa akan mijinki, ki kula da sukarki Bata da damuwa ko kalilan ki girmama Masa danginsa da kakarsa jiya ya wannan suna gidan Nan sunzo ganin Mai sunan mijinki na wurin Sameeru, Ni cewa nake can wurinku zasu sauka ma sai naji Sameeru na maganar su fito zasu koma a jiyan kinsan sha'anin tafiyar iska, ba wani nisa ke gareta ba". Ita dai Zahra Jin Hajiyar take Dan ba komai ta fashimta ba. Rukayya ce ta shigo da Abinci dasu snacks a babban tray tana fadin " Ai tunda naji shiru Hajiya Baki fito ba nasan kin hanata barci kawai wallahi ke idan Kika so Abu ba sauki saina Allah idan kinyi hakuri zata tashi ki bata". "Ke tafi can waya fada Miki ana bori da sanyin jiki Baki San hadarin wannan abun bane baya barin haihuwa fa ba dole a tari abun ba tunda wuri, wannan yarinya tubarakallah haka ai ba'aso a samu abinda ze kawo Mata cikas a zaman aurenta ba, ni tunda na ganta ta kwanta min har maganin tsarin jiki Zan karbo mata a Sanka, nan babban gida". Baki Rukayya ta rike tana kakabin Abun "Ikon Allah to ke Hajiya fada Miki tayi tana son na tsarin jikin? Da kike faman fadin Zaki karbo Mata". Kafin Hajiyar ta Kara magana Zahra ta rigata. "Haba Aunty Rukayya Ina laifin Hajiya kuwa tunda na sako Qafa gidan Nan Bata huta ba hidimata takeyi". "Eh haka ne kam tunda har kasuwar kurmi ta aikeni, da girnana da komai nace bazanj ba tace nayi mata kiwa dan rabon da naje cikin kurmi tun Ina secondary Dan ma ban manta shogon ba" Ficewa Hajiyar tana fadin kyaji dashi idan Kaya ne". Tashi zahrar tayi tana fadin Bari na dawo, ta fice daga dakin. Toilet ta shiga ta Kara gyara Kanta, lokacin data fito dai dai lokacin masu kawo lefen suka karaso suma Nan da nan gudan ya dauki jama'a Dan makota ma Wanda suka makara suka ringa shigowa. Ganin gidan ya kacame da jama'a yasa Zahra tayi amfani da wannan damar ta nufi hanyar soron gidan, a soron ta tsaya ta Ciro wani face mask da yake cikin jakar ta da eyeglasses dinta ta saka ta fice daga gidan. Ba Bata lokaci tana fita Dan sahu Yana kawo Kai, ta dafe shi ta shige, tana fadin "Janbulo zaka Kaini". "Hajiya sai dai drop gaskiya Dan hanyar ta baude ni rimi na nufa". "Muje Zan baka kudin drop din". Ta fada tana Dan leken gefenta kamar narar gaskiya, hankalinta be kwanta ba sai da taga sunyi nisa da unguwar, ajiyar zuciya ta sauke tana "na barka da Dr Sai ku cinye kanku haka kawai za'a sabautani saboda Kai,Wanda har yanzu bansan daga wace bahiyar ka bullo ba, ayi min sakiyar da Babu ruwa a cuceni a cuci rayuwata shi yasa na taho da hirina idan tayi ruwa rijiya idan batayi ba ta Zama Masai" Kafin su karasa layin su Ssjida tacewa Mai adaidaita din ya taya gurin me P. O.S zata ciri kudi. Har kiofar gate din gidan ya kaita 10k ta bashi, cikin mamaki ya dubeta "Hajiya kudin sunyi over dari bakwai ne kudin, Hala ke bakuwa ce?" Gaga tayi Tana fadin na sani kaje kawai nagode Allah ya tsare". "Na gode Allah ya rufa asiri ya kara Miki daukaka". Tana tafiya tana fadin. "Allahumma Amin". Ta shige gidan shi Kuma ya juya Kan mashin dinsa ya wuce Yana Fadin "Bari na koma na sallami gidan sai na Kara fitowa". *********** Bayan tafiyar masu kawo lefen an baje anata kallon kayan arzikin da suka kawo Masha Allah kayansu sunyi kyau sosai Dan akwatuna set hudu suka kawo da manyan jakunkuna uku har da adudu biyu. Saida komai ya lafa sannan hankalin Rukayya ya dawo jikinta ta shiga neman zahra, abin mamaki ba zahra ba alamarta Abu kamar Wasa ya Zama gaske Nan da Nan tashin hankali ya wanzu a gidan Dan mantawa akayi da murnar wani lefe Nan da Nan Rukayya ta Fara share hawaye. Mommy ce ta Farayi Mata fada "Haba Rukayya menene haka Zahra Karamar yarinya ce ku shiga makota Mana ko taron jama'a ne bataso ta shiga can ta zauna ba kince toilet tace Miki zata shiga ba? Kafin ta fito Kuma bakin sun shigo?" "Eh haka ne Amma Naga fitowarta harta tsaya a can daga Nan mutane sukayi yawa ban sake ganinta ba". "Ke Zubaida maza ku shiga gidajen kusa ku duba ko can ta shiga ku kirawota". "To mommy". Ta fada sukayi waje su uku. Hajiyar makwarari kuwa cewa take "Ina yarinyar nan ta shiga ko masu kawo kayan tabi suka tafi". Wani kallo Rukayya tayi Mata "kaji Hajiya da wani zance kamar wata 'yar baby ce zahrar da zatabi wasu mutane". "Ungo Nan". Abu kamar Wasa karamar magana tana neman Zama babba, duk kukkuken babu it's Babu dalilinta komai Kama da Zahra Babu. Mommy da Kanta ta Kira Sameer tace duk inda yake yazo yanzu tana son ganinsa. Daman ba nusa yayi ba Yana tare da abokansa na unguwar Dan a hannun Hajiyar ya girma harya Gama secondary school dinsa. A tsakar gida ya samu su mommy anyi cirko-cirko. "Gani mommy lafiya na ganku haka?". Hajiya ce ta Fara fadar "Ina fa lafiya ba'aga matar Mahmudu ba har makota anbi baku ko alamarta". Mommy ya kalla. "Kamar ya ba'a ganta ba? To Ina ta shiga?" "Allahu A'alam, da farko abin ban dauke shi haka ba sai yanzu da naga da gaske ne yasa nace Bari na Kira ka". "Ok, Bari naje Nan Ina zuwa" Ya juya ya fice da sauri, cikin tashin hankali me ze fadawa Mijinta Ina ta tafi?. Tambayar mutanen kusa masu sana'a a kofar gidan ya rinka yi, har ya juya sai wani Mai sayar da Mai yace yaga fitowarta da face mask da glass a Ido ta hau a dai- daita sahu sunyi hanyar nan ya nuna hanyar gidan shatema. Dafe Kai yayi cikin tashin hankali, "wannan wace irin masifa ce haka kawai an tadawa yarinya hankali har ta yanke Shawarar tayi tafiyar ta, to tana Ina? Ina ta tafi? Ba wani ta sani a garin Nan ba ga Babu waya a hannunta, Saida ya fada masa ya fito Mata a mutum sak a wuce wannan wasan yaran ya kaita inda ya Dace a duba Masa ita amma ya gano ya yiwa Haseena waya ta a duba Masa ita yasan karshen film din ba Mai kyau bane" Jiki ba kwari ya koma ciki.. ***** ***** ***** Hankalin Zahra be kwanta ba so sai Saida ta ganta a cikin falon gidan su Sajida, Mai aikinsu ta bude Mata parlourn tana fadin "A'a marhabin maraba da Amarya sannu da zuwa". Ta fada tana murmushi, tare suka shigo ciki. "Yauwa Mama Hauwa sannu da gida, ya naji gidan naku Shiru ko su Mamar basa nan ne?" "Wallahi sunje Rimin sumaila duba kanin Baffa bashi da lafiya,a nan ya kwanta a Asibitin Murtala to shine sukaje su Kara duba shi da jikin". "Allah sarki ko kawu Musa?" "Shine Ashe kin sanshi". Eh nasan shi Mana, har a gidansa mun kwana lokacin da mukaje da sajida. Allah ya bashi lafiya yasa kaffara ne".. "Allahumma Amin, Bari na bude Miki dakin mutuniyar ki shiga na kawo Miki abinci can, inaga sai dare zasu dawo tunda suka Kai har wannan lokacin". Wanka ta shiga ta Dade a toilet din kafin ta fito tana tsane jikinta da towel, lotion ta shafa ta dauko Rigar material marar nauyi ta saka a cikin kayan sajida. Jallop din kuskus aka kawo Mata wadda Tasha kayan lambu da pepper soup na kayan ciki da kunun aya Mai sanyi da ruwa. Abincin taci ta koshi ta dora da kayan sanyi tayi hamdala ga Allah ta kishingida jinta take fresh idan Allah ya kaimu safiya ta karawa motarta Mai, ganinta a araha yasa ake garata kamar kwallo.AUREN HUCE HAUSHI. MAMAN FATEEMAH Page 42. _______Abu kamar Wasa har kusan karfe taran dare ba zahra ba labarinta, iya Rahane mommy ta Kira tana tambayarta kosu Rukayya sun dawo? Dan bazata fada ba direct tace ana neman zahrar hakan dabara ce ta tambaya a fakaice. Amsar data Bata ita ta Kara tadawa kowa hankali cewa tayi "Basu dawo ba tun fitar safe da sukayi ga zulai ma duk ta shiga damuwa tace tun yamma Ammarta ke Kiran wayar zilan tace wayar zahara'un Bata shiga". "Yanzu ya za'ayi kenan?" Rukayya ta tambaya. "Ni damuwa ta Daya kada ta fada mugun hannu Dan ma dai ba lallai ansan matar waye ba Amma yau abin tsoro ce kiransa zanyi kawai na fada Masa halin da ake ciki ko yasan wasu 'yan uwansu a nan kanon, tunda barin Kashi a ciki baya maganin yunwa gara ya fada kawai asan Yanda za'ayi tun guri be kure ba. Number dinsa yayi ta try Amma amsar Daya ce a rufe take. Da kyar ya mayar dasu mommy gida har Rukayya a gidansu ta sauka, to ta koma tacewa baiwar Allah da sukazo tare zahrar ta Bata ko me?" Duk wani lissafi ya gama suncewa Sameer, duk wannan Abu be tashi faruwa ba Saida sukazo gidan kakarsa, ita kanta Hajiyar makwararin tashi Dan kukanta tana mitar yarinyar Nan Bata kyauta Mata ba ta rasa a inda zatayi irin wannan shegantakar sai a gidanta. Jiki ba kwari Sameer ya shiga gidansa, sau Daya Fateeha ta kalleshi ta dauke Kai ta cika fam da fushi tun safe Daya fice Bata Kara sakashi a idanunta ba, ta kirawo shi ya Kai sau biyar sai dai yace Mata gashi Nan Amma bezo ba sai yanzu wurin Sha dayan dare. A kusa da ita ya zauna ta kauda Kai, hannu yasa ya dauki yaron a Kan cinyarta, yasa hannu Daya ya tallabota ta hada da babyn ya rungumesu, Jin ajiyar zuciyar da yake saukewa a jajjere yasa Fateeha ta gane da matsala. "Wai menene?" Ta fada cikin damuwa. "Bari kawai wlh hankalina a tashe yake, tun bayan Azzahar Zahra ta fice daga gidan Hajiyar makwarari bamu San inda ta nufa ba, duk inda muke tunanin zataje munje Bata nan". Itama mantawa tayi da fushin da takeyi dashi ta Fara sallallami "Yanzu Ina ta tafi? Kadafa wani Abu ya sameta kasan mutane yanzu gaskiyar su kadan ce". Dafe kansa da yake Sara Masa yayi "Bana tunanin haka gaskiya da Kanta ta fita ta tafi kawai dai an Bata Mata Rai ne ban Kuma yi tunanin abin yayi Mata zafi haka ba da bazan barta a gidan Hajiyar ba, amfani tayi da masu kawo lefen mujahida ana can gurin karbar lefe ita Kuma ta fice daga gidan Dan akwai Wanda ya fada min Yanda ta fito nasan da niyya ta fice abunta". Zuru Fateeha tayi tana sauraren mijinta. "Ka Kira ka fada masa?" Kai ya girgiza Yana fadin na kasa samunsa nafi one hour Ina nemansa ban same shi ba". *** *** *** *** Karfe Tara su Umman sajida suka shigo gidan lokacin Zahra na parlour suna hira da Mama Hauwa, turus Maman tayi ganin zahra ko rantsuwa tayi Babu kaffara, wannan ba zuwan arziki bane amma sai ta share tana fadin "wa nake gani haka?" Dariya Zahra tayi tana fadin "Umman mu sannunku da hanya". "Yauwa sannu,aike za'a yiwa sannu kin sha doguwar tafiya". Shiru zahrar tayi batace komai ba, kannen Sajidar ne suka Fara gaisheta suna fadin "Aunty kin rigamu zuwa munata cewa idan Ya Abba ze Kai Miki sakonki da Baffan Rimi ya bada a Kai Miki zamu bishi sai gashi Kuma kinzo" Karamar kanwarsu ta janyo tana fadin "ai zakuje ko mutuniyar tunda anyi min Alkawarin zuwan". "Eh zamuzo Aunty zahra". Nusaiba ta fada suna Zama kusa da zahrar, yayin da Maman su ta wuce bedroom dinta tana cike da tunani barkatai a zuciyar ta. Tana shiga jakar hannunta ta zuge ta Ciro wayar ta, Ammah ta Kira Dan bazata Zama uwar banza ba da alama gudowa yarinyar Nan tayi. Lokacin da Kiran ya shigowa Ammah tana duba wasu kaya da Hajiya kaltume ta Aiko Mata dasu ne. Ganin Umman sajida ne yasa ta aje kayan ta dauki wayar tare da sallama. "Wa'alaiki Salam warahamatullahi ta'ala wabarakatuhu". "Hajiya ya gida ya wajen Amare? Ina ta son na Kira mu gaisa Allah Bai nufa ba sai yau, itama zahrar mun kwana biyu bamu gaisa ba". "Wallahi kowa lafiya, Amare Kuma suna nan kusa daku Bata jin dadi ne mijin ya matsa suzo Nan Kano a dubata ni tun safe da muka gaisa da wayar zilai ban Kara samunta ba, na Kirawo zilan ma tace min har yanzu Basu dawo ba duk ta tada hankalin ta, nace ita da ba ita kadai ta fita ba tare suke da amininsa da kanwarsa, Kinga duk inda suke ai suna tare". Shiru Maman tayi kenan hasashenta ya kusa Zama gaskiya Kenan. "Hajiya ga zahrar a gidan nan,yanzu muka dawo daga Rimi Sai na tarar da ita Ina ganinta nasan ba lafiya ba Ashe garin sukazo ta kawo min ziyara". Jim Ammah tayi tana jinjina lamarin. "Anya kuwa ki dai saka Mata Ido zuwa safe kome ke nan sai ki fada min idan anzo daukarta to da sanin mijin tazo idan Kuma tace zata tafi ki hanata ki fada min na gode kwarai Allah yayi Mana jagora ya Raya Mana zuri'a". "Allahumma Amin". Sukayi sallama. Zuciyar Ammah sai bugawa takeyi a hankali ta furta "meke Nan Kuma? Ni Asma'u Allah ka taimaki 'yar marainiyar Allah, matsaloli daga an toshe wannan sai waccen ta bulle Allah yayi Mana maganin wannan matsaloli yanzu kuma ko menene damuwar datasa ta tsallake tabar inda suke gashi ta Kama wayar ta rufe Dan ma kada a San inda take,ai kuwa zamu gauraya bazan dauki shashanci ba". Ta hada duk kayan ta zuba a ledar da aka kawosu ta fice daga dakin ta nufi dakin Abban Yara tunda ita keda girki. Saida Umman sajida tayi wanka tayi sallah sannan ta fito har lokacin suna falon da yaran direct dining ta nufa taci abinci sannan ta dawo falon. Gaisheta zahra ta Karayi tana tambayar ya Mai jikin, Dasu Baffa. Sun dauki lokaci suna hira kafin Ummar tace "Wai daga Ina kikazo ne daga can Azaren ne ko Kuma kinzo nan garin ne?" Shiru zahrar tayi kafin tace "ganin likita nazo akan wannan ciwon marar da bakeyi duk wata". "Ikon Allah kuma ke kadai Kika taho ganin likitan kamar marar gata". "A'a bani kadai nazo ba tare da Aunty Zilai Mai aikin Ammah mukazo tana can a Nasarawa G.R.A". "Ok, to mryasa baku taho tare ba Nan din". Shiru tayi Bata ce komai ba, ganin da Yara yasa itama ummar tabar zancen. Kafin kowa ya tashi Zahra ta tashi tana fadin "Umma Bari naje ba kwanta barci nakeji" "To Allah ya tashemu lafiya. Basu Dade ba Suma suka shige daki Daman duk sun gaji. Lokacin da Ammah ta shiga dakin Abban samun Mama tayi kane -kane tana ta zuba zance da kudi a hannunta masu Dan yawa da gani a gurin Abban ta Karba, cikin alamun rashin gaskiya mamar ta Fara fadin. "Aina leka parlourn ki naji Shiru nayi zaton kina Nan wallahi Ashe Baki shigo ba" Fuska ba annuri Ammah tace. "Eh ban shigo ba idan kin gama na dawo ta juya har Takai kofar ficewa Abban yayi gyaran murya Yana fadin "dawo ki zauna Ina Kuma Zaki ita ta tashi ta tafi tunda ta gama abinda ya kawo ta" Jiki ba kwari Mama ta tashi tana fadin "ai Kam na Gama Allah ya tashemu lafiya nagode Allah ya Kara arziki". Ta nufi inda Ammah ke tsaye tana fadin "mu kwana lafiya ki tayani yiwa Abban yara godiyar abin arzikin Daya bawa Najjahi na kudin registration". "Masha Allah! An gode Allah ya bada sa'a". Ta fada fuskar ta Babu walwala ko alama, da gaske ta kule Abun Yana so ya Zama rainin hankali tayi noticing dinta duk ranar girkinta sai ta dunga Karakaina a part din Abban Amma idan tasan wata ai Bata San wata ba. Dawowa tayi ta zauna kusa dashi "meya Bata Miki Rai ne Kika juya Zaki bar dakin?" "Ba komai". Ta Bashi amsar in short. Haka Nan yabar zancen badan ya gamsu da abinda ya fada ba. "Neman izinika na shigo zanje Kano gobe in Sha Allah".. Saida ya Kare Mata kallo tsab sannan yace. "me akeyi a kanon da zakije?" Kai ta girgiza ba komai zanje barka ne na yaron nan Sameer ranar da yazo daukar su Zahra yake fadawa magaji anyi Masa haihuwa an samu takwaran mijin Zahra". "Kai Masha Allah, ai ban sani ba da nayi Masa barka ranar da yazo". Tashi tayi zata fice Abban ya mayar da ita "Wai me yake faruwa ne Naga ranki a bace tun shigowar ki". "Ba komai zanje na dawo ne yanzu in Sha Allah". Ta Mike ta nufi kifar ficewa, haka Nan yayi Shiru badan ya yarda da ba yasan da abinda yake damunta taqi fada Masa ne kawai". Ammah na shiga part dinta ta Kirawo Abdul Hakeem, lokacin Yana kofar masallaci tare da Habib. A parlour ya samu Ammar ta zuba tagumi. Saida yayi sallama biyu sannan taji. "Wa'alaika Salam". Ta fada tana kallon Abdul Hakeem din, kusa da ita ya zauna Yana fadin "lafiya kuwa Ammah Ina sallama bakya jina?" Ajiyar zuciya ta sauke tana fadin "yanzu ba dadewa Umman Sajida ta kirani waiga zahra taje Mata zata kwana a can Kuma ita kadai ba tare da zilai ba, na Kira zilan tace min tun fitar safe Basu dawo ba har dazun, ka Kira Sameer kaji shin yasan da tafiyar ko Kuma wani Abu ya faru tayi musu yqji nasan halin kayana zatayi abinda yafi haka ma in dai zahra ce, Dan haka ka kwana da Shirin Kano sakko zamuyi ko Abban KU ban fada Masa wannan maganar ba ina tsoron ta fito duk da nasan ba lallai ta fito din ba amma sha'anin mace da miji sai Allah" "Allah ya rufa asiri". Abdul Hakeem ya fada Yana Kiran Sameer duk da lokacin ya ja Sha Daya ta gota. Ringing Daya saneer ya daga kafin Abdul Hakeem ya Fara magana Sameer ya rigashi Dan ko sallama Babu ya Fara fadin "Abdul Hakeem zahrar tazo Nan ne?. "Easy my man! Tana Nan Kanon a Janbulu gidansu Sajida, yanzu Umman su sajidar ta Kira Ammah ta fada Mata saboda hankalin ta be kwanta da ganin zahrar ba duka yaushe akayi Abu da zata wani zo yawon ziyara tasan da wata a kasa, shine ta Kira zilai ta fada Mata tun fitar safe baku dawo ba". Ajiyar zuciya ya sauke, sai Yanzu ya samu nutsuwa dan Yanzu suka gama wayar da mommy akan ko akwai wani cigaba? Yace Mata Babu Kuma tun lokacin da abun ya faru yake ta kokarin ya Sami Mahmud Abun ya faskara. "Na gode kwarai Abdul wallahi muna nan hankalin mu a tashe tun bayan Azzahar muke Abu Daya, Dan Allah kayi min godiya gurin Ammah, kace Kuma tayi hakuri ba sai tazo ba Dan Allah ga mommy ta Isa tayi komai ka fada Mata laifi akayi mata amma in Sha Allah hakan baze Kara faruwa ba wannan ma tsautsayi ne". Kai kawai Ammar ta gyadawa Abdul Hakeem ya gane me take nufi tunda handsfree ya saka wayar". "To ba damuwa tace ayi maka godiya da kwaramniya" "Ba komai yiwa Kaine ka turo min da address din gidan Yanzu na gode". Sukayi sallama ta kashe Kiran Yana Maida hankalinsa a Kan Ammah. "Ammah lokaci yayi daya kamata a zauna da Mahmud asan who's he? Aure ba Abun Wasa bane asan asalinsa Kinga muna tare sosai wallahi be taba fada min asalinsa ba kawai dai nasan he's educated fiye da tunanin mu badai ya nunwa ne kawai anyway kome Kenan dai kiyi abinda ya kamata kawai". *** **** *** Suna Gama waya Sameer ya lalubo Number Rukayya tana dauka yace ki fadawa mommy gani Nan zamuje mu taho da Zahra tana janbulo gidansu friend dinta". Bai jira tayi abinda zata fada ba ya katse Kiran ya saka jallabiya ya dauki key din motar yayi waje. A kofar parlour ya tarar da Rukayya da Mommy. Fitowa yayi yana fadawa mommy Yanda sukayi da Abdul Hakeem da Ammah. "Dan Allah ki zauna mommy muje da ya Sameer kawai ana ganin mu dake za'a San ba lafiya ba Kinga ai itama zato takeyi kawai muce Mata ya Mahmud ne ya dawo yace muzo mu taho da ita tinda da saura lokaci". "To shigo mu tafi tsari mistress". Saida suka dauki titin rijiyar zakin sannan Sameer ya mikawa Rukayya wayar da address din da aka turo Yana fadin " duba ki gani ko kinsan laying kune masu yawo lungu da sako na garin nan". Dubawa tayi tana fadin " Nasan gurin layin gidan su saliha sani Musa ne tare mukayi Excel da ita". Cikin ikon Allah suna tsayawa a kofar gate din motar ya Abba ta shigo shida Abie dinsu sun dawo daga kwangwalam bodar NIGER inda sukaje gaisuwar mahaifar amininsa data rasu jiya, sun biya ta kazaure gurin wani abokin aikinsa daya kwanta a Asibiti Shima a Nan sukayi dare. Ganin mota a kofar gidan yasa Abie yace Abba ya tsaya yaje yaji ko lafiya Yana fita Mai gadi ma ya fito Yana ganin Abba ya karasa gurin da sauri, fitowa Sameer yayi ya tarbesu Yana Mika musu hannu sukayi musabaha Yana fadin "Ayi hakuri munzo cikin dare ba sanarwa,Daman munzo mu tafi da zahra ne tun Rana tazo Bata Fadi zata kwana ba sai Yanzu mijinta ya dawo gashi ba waya a hannunta, ganin da sauran daren yasa muka biyo samunta". ,"Ok. Ba damuwa muma Yanzu shigowar kenan munje unguwa tare muke da Abie". "To mu karasa Mana na gaishe shi ya juya yabi bayansu suka nufi gurin Abie din, Rukayya gani tayi kamar akwai rashin kyautawa ace tana kallo aje a gaishe da babban mutum tana zaune sai kawai ta fito ta rufa musu baya. Cikin girmamawa Sameer ya gaishe da Abie din sai Jin muryar Rukayya sukayi daga baya tana gaishe da Abie din, hankalin Ya Abba biyu ya kasu ga wata murya data fizgeshi lokaci Daya ga Kuma bayanin da yake yiwa Abie. ""Ba wani Abu Bari a Kirawo Umman tasu saita fada Mata ta fito wannan ai shashanci ne ya za'a bar yarinya ta nemi gurin kwana da mijinta da komai". Sameer ne ya Dan shafa Kai. "Ayi hakuri Abie mijin ne baya Nan sai yanzu ba dadewa ya shigo kasar". Mazaunin direba Abban ya koma suka nufi ciki tunda Daman Mai gadi ya bude gate Yana jiran su shigo. A waya Abie ya Kira Umma har lokacin idanunta biyu da wuya tayi barci matukar tasan mijinta baya Nan da sauri ta dauki wayar tana Masa sannu da zuwa. "Yauwa ya amsa a takaice Yana fadin. "ki taso bakuwar da kikayi a gidan mijinta ya dawo gasu Nan a gate". Ya kashe Yana nufar part dinsa. Shiru tayi waye ya fada masa da bakuwar a gidan jiki ba kwari ta nufi dakin sajida, barci ta Samu tanayi sadidan kamar Nan duniya Bata da damuwa Kota sisi dakin ta shigo tazo bakin gadon ta tsaya tana Kiran sunan ta a hankali, tana fadin "tashi ki kimtsa ki fito ga Mai gidanki can zaku tafi gida". Idanun tadan zaro tana fadin "wallahi bazani ba Umma kice musu bana nan sai hawaye".. AUREN HUCE HAUSHI. MAMAN FATEEMAH. Page 43. _______ kuka zahra keyi ba kakkautawa a hankali Umman ta zauna kusa da ita, ki daina kukan Nan kiyi hakuri ki tashi ku tafi, kiyi ta addu'a Allah ya kawo Miki saukin ko menene damuwar, kada ki Kara tunanin yin irin haka idan Abu ya dameki ki tafi kibar gida ba shine maslaha ba kinji, tashi ki cire Rigar barcin ki canza suna jiranki Kinga dare ya farayi inaga tun Rana suke bulayin nemanki sai Yanzu suka samu inda kike". Kai ta gyada tana goge hawayenta, Bata taba tunanin yau zata koma gidan Nan ba Dan ita a budget dinta daga Nan gaba zatayi Dan kasar tayi niyyar tsallakewa tayi gaba abunta tunda passport dinta yana jaka, to Wai ta Yaya suka gano tana gidan Nan Wama yasan gidan a cikinsu, to shi yaushe ya dawo? Haka zuciyarta ta dunga sake-sake. Fita Umma tayi ta Bata guri ta canza Kayan, jiki a mace ta fito ta iske Umma da Ya Abba a parlourn, gaishe da Ya Abban tayi ya amsa Yana fadin "wallahi kin wahalar da mutane da wannan Daren Kika sakasu fitowa har da mace Ina jinma mijinta ne" .ita dai zahra Shiru tayi Masa ta nufi Hanyar fita daga parlourn tana fadin "ummah na tafi Saida safe". Ta fada tana yin gaba "to Allah ya tashemu lafiya kiyi hakuri da safe idan Allah ya kaimu ki bude wayar zamuyi magana". "To Ummah in Sha Allah Zan bude". Suka fice daga Fallon. Ya Abban Yana biye da ita tun kafin ta karaso Rukayya ta taho cikin sassarfa ta ringume Zahra tana fadin "wallahi kin dauki alhakina da Hajiyar makwarari Kinga kukan da muka Sha yau? Tambayi Ya Sameer kiji duk kin tashi hankalin mu". Wani sanyi ya ratsa Ya Abban Jin Rukayya ta ambaci Sameer da yayanta, daman Kuma yaga Kama ta zahiri duk da dare ne Bai Hana shi ganin kamannin nasu ba. Shiru zahrar tayi Mata ita sai Yanzu taji wata kunya duk ta rufeta, me kenan tayi? Shike Nan zasu dauka fa tayi yaji ne dole ta magantu. "Wai Dan Allah Aunty Rukayya ku kasa barina nayi kwana ko Daya ne a gurin Ummata nifa bada wata manufa ba na taho kawai dai nasan idan nace zanzo ba Bari Oga sameer zeyi ba zece saina nemi izinin....." Sai tayi Shiru. "Izinin wa za'ace ki nema?". Gaba tayi kawai ta nufi gurin da Sameer yake tsaye jikin kofar driver, da wannan damar Ya Abba yayi amfani ya matso kusa da Rukayya yana fadin "Ashe Aunty tasha kuka zanso Naga kina matse hawaye". Kallonsa tayi haka nan taji yayi Mata kwarjini. 'yar dariya tayi tana fadin "Ina yini?" "Lafiya kalau beauty, ki saka min number ki Zan kira naji ya kukaje gida tunda sister Zahra har wayar tayiwa tawaye". Ya karasa Yana murmushi itama murmusawar tayi tana karbar wayar, number ta saka Masa ta Mika Masa wayar tana fadin "bari na wuce ya Sameer Yana jirana" Tayi gaba. "Ok saina kira shima gurin Sameer din ya nufa sukayi sallama, ya leka ta window Yana yiwa Zahra magana. Tunda suka dauki hanya ba Wanda ya Kara magana sai ajiyar zuciyar Zahra ke sauka kadan- kadan. A hankali zahra ta bude Baki tace "Dan Allah oga sameer kayi hakuri na Bata maka Rai bada niyya nayi ba kawai dai Ina son Naga Ummah ne Naga kuma kamar bazaka yarda naje na kwana ba". "Ba komai kawai, Daman Yanda su mommy suka tada hankalin su ne ya daga min hankali nasan ba Bata zakiyi ba tunda da kafarki Kika fice". Shiru tayi tasan magana ce ya fada Mata a kaikaice, tasan a kule yake da ita kawai dai Batasan dalilin Daya hana yayi Mata buyaji ba, Dan taga alama ya iya tijara Yanda ya karewa Rukayya dazu ko shi yasa taja bakinta tayi shiru Yanzu. Sha biyu da minti goma yayiwa Mai gadin gidan horn Saida ya leko shima Sameer din ya fito Yana ko waye sannan ya bude. Yana shiga da motar Maimakon yaje kofar main parlourn sai taga yabi ta baya ya nufi wani gani Mai azabar kyau ko Ina tar kamar dauko ginin akayi aka aje ga wata 'yar baranda data hade ginin biyu an saka glass anyi kamar katanga da wasu irin flowers masu kyau a jere ana ganinsu gurin yayi matukar kyau da burgewa a kusa da steps din da ze sadaka da Main parlour, Zahra ba tayi kokarin bude side din da take zaune ba, dan juyowa Sameer yayi "Dan Allah kada maganar nan ta fita kawai da safe ki fada musu mun Dade a Asibitin ne yasa Kika bamu dawo da wuri ba sun kulle, kiyi using da Nan kawai ki barsu su a can, Rukayya zata kawo Miki kayanki da safe kiyi idan Allah ya kaimu". "To nagode". Abinda ta iya fada kenan, ta bude ta fita Rukayya man ta fito tana fadin " Bismillah kizo muje na rakaki". Tare suka jera suka hau zuwa kofar, ita Kanta kofar abin kallo ce ita Yanzu zahra abin har ya daina Bata mamaki so take taga iya gudun ruwan bayin Allah nan Kullum lamarin su ba baya yake ba gaba yakeyi daga Nan sai can suna shiga ta Kara jinjina girman lamarin Wai shi wannan abokin nasu wane irin kusancin ne a tsakanin su da za'a dunga sauke ta a duk inda akayi ra'ayi. Wannan part din yafi wancan komai parlour sun Kai hudu, a cikin parlour na uku ne suka taka steps ya Kai shida sannan suka shige want korido ko Ina tadal sai wani special kamshi ke tashi bedrooms ne guda biyu a jere, Rukayyar ce ta Dan juyo tana murmushi "to madam gasu Nan saiki shiga Wanda kike so ki kwanta, tunda kin samu muna yawon dare kamar marasa gaskiya, Zan Baki shawara sai kin Zama jaruma fa a gidanki Dan Ya Mahmud wallahi Mata rubibinsa suke, idan kikace Abu kadan Zaki fece kece ki tafi kece a kwana Dan idan yayi wata tafiyar sai ki kwana hamsin Baki saka shi a idonki ba, pls you have to be very strong gaskiya kada ki yarda a gano Ina kike da lapse akwai damuwa kwarai ki rike mijinki da kyau ki mutunta shi ki girmama iyayensa zakiji dadin Zama dashi in Sha Allah, zabi na rakaki dakin na wuce barci Kuma nakeji tunda Allah yayi Mana gyadar dogo ya rabamu da kwanan zaune to matar big bro ta Bata Ina Ni Ina barci ai sai kwana sallah". Ta fada tana 'yar dariya. "Ki sakani kowanne Wanda za'a sanwa ya taba cewa way gutsiri nan? Duka zaman na yau zuwa gobe ne Dan gida zamu koma bana son wani surgery a Nan idan ma yimin din za'ayi ba wannan Mai fuska kamar Jan karas din zatayi min ba muma muna da qualified a can Dan dai kada nayi musu dashi ne kawai". "Kinga mu Shiga na koma dare Karayi yakeyi gara naje na kishingida". Dakin da yake facing dinsu ta bude MashaAllah" ta fada Tana karewa dakin kallo sannan ta juyo tana fadin mu kwana lafiya" Kallonta Zahra keyi tana son tayi Mata tambaya Amma ta rasa ta Ina zata Fara, Dan Yanda tasan gudan Nan da Yanda take fadar wasu abubuwan akan Mahmud ga Kuma abinda Hajiya kakarsu ta fada Mata dazu maganganun suna kamanceceniya da juna amma Bari ta Adana tambayoyinta da sauran lokaci. "Nagode Aunty sai da safe, Amma fa Ina Jin tsoron gurin nan fiye da can din wallahi, Kinga Nan ba kowa. Allah mu kwana tare ko kin tafi bazan iya barci ba". Dan Jim tayi tana tunani ita Kanta Bata San dalilin Ya sameer na kawota Nan ba, amma tasan dole da dalilinsa nayin hakan. "Ok ba damuwa Bari naje na dauko sleeping dress Dina da naki saina dawo" "Ok, yauwa Aunty ki taho min da phone Dina tana cikin bedside". Ta nufi Hanyar fita, wayarta ce ta dauki ringing number ce tasan Wanda ya Karba ne dazu a ta daga da sallama suka Kara gaisawa ya tambaye ta ya suka zo gida ta fada masa lafiya kalau sukayi sallama ta fice. Kofar ta rufe ta farko tayi gaba tana fadin "kamar wata Rukayyar mahaukata na shigo wannan part din na kwanta a can ma naki kwana ballentana a Nan yarinya Allah ya kawo mijinki ki tarairayi kayanki kuna gefe Naga alama sai nayi Mata budedden karatu sannan zata gane mace har Mace ta fita kunya Amma ki tsaya kina Wasa da damarki". Ta wannan barandar Mai glass ta Shiga Daya part din da yake tasan wanancin lambobin kofofin tunda duk sati suke zuwa da sauran yaran gidansu suna gyara bedrooms din kawai sauran Kuma da masu aikin da sukeyi dakunan kwanan ne dai Batasan dalili ba masu aiki basa shiga. Ko Ina tsit a gidan baka Jin komai sai kukan kananun kwari da dai daikun tsuntsaye ta gefen inda zahrar ta kwana ta wuce da gaske ko ita data Saba da Shiga gidan wani lokacin tsoron Yana kamata bare a irin Nan da sauri ta shige parlourn na uku ta wuce corridor da za sadata da dakunan. Tana bude dakin zilai ta bude ta fito tana fadin "sannunku da dawowa, Dan Allah lafiya kuwa tun rana sai Yanzu sha biyu ta wuce?'. "Lah ba wani damuwa munje unguwa ne motar ta samu matsala sai dazu muka shigo garin muka biya gidan mommy a can muka Shantake Sai Yanzu ya Sameer ya kawo mu". Wani sanyi zilai taji a ranta, "to ai shikenan Allah huta gajiya da ko barci na kasayi ina ta tunani barkatai". "Kai haba ba komai Allah ya tashe mu lafiya ta bude kofar ta shige itama Zilan ta Koma ciki. Tun bayan fitar Rukayya zahra ta dosana gefen ta zauna ta zabga uban tagumi, da sauri tashi ta fito ta dauko handbag dinta ta biyo Hanyar da suka shigo kofar fitar ta murda tajita bam ko motsi batayi, tayi tayi taji kamar tana taba dutse, hakuri tayi ta juya sai lokacin tsoron ya rufeta da gudu ta shige dakin tana turo kofar, dube-duben makulli kofar ta Farayi ita dai bataga gurin wani key ba har zata hakura taga wasu numbers a jikin wani Abu kamar switch din kunna wuta numbers din ta Danna Yanda suke a jere taba taba ta karshe taji want Dan sound daga jikin kofar handle din ta Kama zata bude taji ta rufe gam, sai lokacin ta Dan samu peace of mind, ta nufi gadon ta aje jakar a gefe ta nufi toilet dole saita sake gyara jikinta. Tana Shiga ta cire rogar material din sajida data sako ta taho da ita ruwan zafi ta hada tayi wanka ta fito da towel a jikinta sanin ba wasu kayan sakawa a Nan yasa ta Haye gadon daga ita sai towel ta rage hasken dakin ta janyo lallausan bargo ta rufe jikinta sai fuskar kawai ta Bari a hankali ta Fara Addu'oin kwanciya barci, kafin ta Gama barcin yayi awon gaba da ita. Karfe Daya da rabi daidai jirgin Max air ya sauka da duban jama'a daga kasahe daban daban na duniya, cikinsu harda Muhmud Muhammad Dange, a hankali yake tako stairs din jirgin sanye yake da kananun Kaya Ash T- shirt da black jeans a jikinsa sai jakar laptop dinsa a kafadarsa. Yana karasa saukowa wani matashi fari marar jiki ya nufe shi Yana fadin "barka da sauka yallabai, ga key din motar Nan a hannunta oga yace na kaika gida, sai Balarabe ya bimu da wata motar sai mu dawo tare dashi". Hannu ya mikawa Mai bayanin Yana fadin "bani key din kawai kace masa na gode kwarai da kulawasa, zanyi driving da kaina". Mika masa Yana fadin "Allah ya tashemu lafiya kayi min godiya sosai ya Ciro kudin America ya mika Masa sannan ya bar gurin. Lokacin Daya fito daga airport din Daya da minti ashirin da bakwai, tuki yake cikin nutsuwa sau biyu kawai ma'aikata suka tsayar dashi, har yazo gate din gidan ba Wanda ya Kara tsayar dashi, sau Daya yayi Horn Mai gadin ya falfalo da gudu yana leken waye a Nan baisan motar ba Dan haka ya koma ya dauko abinda ze Bashi kariya. Kafin ya bude ya fito, Mahmud ya fito ya harde hannusa a kirjinsa ai Mai gadin Yana ganinsa yayi sauri ya koma da gudu Yana Fadin "barka da sauka fari Mai farar Aniya Allah ya Kare gabanka da bayanka baya Mai goya marayu" Dan murmusawar Mahmud yayi Yana fadin "wani Abu sai Malam Musa shi Babu ruwansa da dare". Ya fada Yana kunna Kai harabar gidan wadda take kamar rana, mutane hudu ne suka bullo daga mabambantan gurare. Parking lot suka nufa sun San Mai gidan ne tunda suka jiyo hargagin Malam Musa. Shima da gudu ya karaso gurinsa Yana cigaba da Yi Masa kirari. Sun gaisa sosai dasu har kusan minti biyar sannan yayi musu sallama Saida safe ya nufi babban part din, Murtala ne yayi sauri ya sameshi "yallabai Ina ganin madam din kamar tana can sabon gurin can Dan Nan Naga Sameer ya ajesu dazu ita da Rukayya kanwarsa, can ya nufa Yana mamakin me yasa Sameer ya kaita can alhalin yace a barta a tsohon part din. AUREN HUCE HAUSHI. MAMAN FATEEMAH. Page 44 _________ kamshinta ya Faraji Yana shigowa parlourn, wani limshe idanu yayi Yana ayyana abubuwa da yawa a ransa, direct ya wuce bangaren bedrooms din Yana jinsa cikin nishadi, wato Sameer Yana expecting dinsa ne a kasar shi yasa ya bude Mata nan kenan, a hankali ya taba handle din kofar farko ya jita a bude Shiga yayi komai tsab, iska ya huro daga Bakinsa ya aje jakar laptop dinsa a Kan sofa da take dakin, ya zauna a gefe Yana cire takalman kafarsa, wanka yake son ya Fara kafin ya Shiga gurin waccen danger girl din "yar yarinya ta Hana shi sakat duk ta birkita Masa Lissafi" ya fada a fili Yana rage kayan jikinsa. Wanka ya shiga bai wani dauki dogon lokaci ba ya fito saboda dare ya Fara nisa ga gajiyar zaman guri daya, pyjamas ya saka masu kalar sky-blue ya fesa turarensa ya dauki wayoyinsa ya fice daga dakin ya nufi dakin da zahrar take, wani Abu ya taba mai Kama da socket din electric na kunna wuta sai kofar ta bude,a hankali ya shige Yana Jin kamshinta yanda ya cika dakin, shi dai yawanci duk matan da suka zamar Masa dolensa suna bala'in son kamshi, yana ida shigowa kofar ta rufe Kanta Wai Abu ya taba ba Wanda zahra ta taba ba, yayi gaba Yana nufar gadon inda ya hangeta ta kudundune cikin bargo, da gani a tsorace tayi barcin, wayoyinsa ya aje a Kan bed side ya zauna a gefen gadon Yana Kare Mata kallo, shifa duk hankalinsa ba a kwance yake ba tunda aka fada masa matsalar dake damunta yaji ba shida sauran nutsuwa idan ba zuwa yayi ya ganta ba, Kuma Dole ma yasan abinyi akan ciwon Nan ko ana Wasa da wasu lamuran Banda lafiya baik'i tasan kowaye shiha a wannan lokacin dole ya dauketa ya kaita inda za'a dubata Masa ita duba na gaske. Remote din AC ya dauka ya rage gudunta dakin yayi sanyi da yawa duk da Yana son sanyi amma wannan yayi yawa, a hankali ya saka hannu ya janye bargon daga fuskar ta barcinta takeyi shower cap din dake Kanta ta cire sai gashi Baki sidik Yana ta walqiya a cikin Dan hasken data Bari a dakin, Kara zame rufar yayi har zuwa kirjinta jikin sai wani glowing yakeyi Jin sanyi Yana shigarta yasa ya juyo da fuskar ta inda yake zaune "ya Salam". Ya fad'a a hankali, gani yayi ta Kara yi Masa wani kyau na musamman, Kare mata kallo yayi yaga daga ita sai towel a jikinta, murmushi yayi da gani Batasan da Kaya a dakin ba. Kayan jikinsa ya cire ya Zama daga shi sai boxer short ya shige jikinta ya janyo lallausan bargon ya rufesu Yana sauke ajiyar zuciya, a cikin barci taji an rungumeta gaba dayanta jikinta ne ya dauki rawa shikenan tasan tata ta Kare shi yasa suka nemota da tsohon dare suka kawota Nan Yan ko wane irin ihu zatayi ba Mai jinta, cikin murya Mai rauni tana cracking ta Fara farin "innalilllahi na Shiga uku wayyo Allah na.... Bata katasa fadin abinda tayi niyyar fada ba taji yace "shittt...Ni ne fa cool down precious ba abinda ze sameki a cikin gidan Nan sai ikon Allah, akwai kyakykyawan tsaro". sansanyan kamshin turarensa ne ya shiga hancinta, kokarin kwace jikinta takeyi Dan yayi Mata kane-kane so take taga zahirinsa Amma ya Hana hakan, ita mamakinta Daya yaushe yazo garin kuma ta Ina ya shigo Dan ita dai tasan ta rufe kofar nan. Dai dai kunnenta ya saka Bakinsa "ki kwanta muyi barci na gaji da yawa kin hana duniyata kwanciyar hankali kina min kisan mummuqe ko wayar ma kin haramta Mana yinta, tunda Naga alama Nima Mai laifi ne". Ya fada yana shafa gashin kanta zuwa bayanta, hannu Daya yasa Yana zare towel din data daura a jikinta da sauri ta rike tana girgiza Masa Kai. "Dan Allah ka Bari bafa kyau muyi barcin to". Wani guri ya taba a jikin gadon wasu irin fitilu suka Kama kamar star masu haske sosai, Bata ankara ba ya fizge towel din gaba Daya daga jikinta Yana Mata wani mayen kallo hannu tasa ta kare kirjinta cikin matsananciyar kunya tace Masa "Dan Allah ka kashe hasken Nan wallahi kunyarka nakeji". "Ni kike Jin kunya?" Kai ta gyada Masa, 'Well done Yanzu kuwa Zan cire kunyar nan daga idonki". Wani bed sheet data gani a gefen gadon ta janyo da sauri ta lullube jikinta dashi tana Kara sadda Kai kasa Dan da gaske ya saka taji kunya sosai. Wutar ya kashe ya matso sai Jin mutum tayi ya shigo cikin Bedsheet din data rufa dashi ya hanye shi ya maye gurbinsa da lallausan bargon. "Ki hanani Zama a gurin neman abincina sannan na dawo ki Kama guduna, ai impossible wallahi muyi barcin da safe mayi bayanin". Ya Kara mannata a jikinsa suka samu body contact da kusancin zahiri. Sun jima yana sarrafata.Tayi laushi iya laushi dan da gaske da kishirwarta ya shigo garin tamkar mayunwacin Zaki badan tana cikin rashin tsarki ba da Babu abinda ze Hana labarin sauya salo, dan tuni ya wani manta da Alkawarin da ya daukarwa Kansa, Saida tafiya tayi nisa ya ji abinda yayi Masa cikas Dole ya saurara Mata, sun kai kusan karfe uku da rabi a haka shi Mai fad'ar barci ya keji sai gashi ya bige da Hana Mai barcin yin Bata barcin. Sai sauke ajiyar zuciya suke su duka har lokacin hannunsa Bai daina shafe shafe ba, wani irin yanayi jikinta keyi har mararta ciwo ta Dan Fara Mata cikin dashashshiyar murya mai dauke da salon shagwabar da Batasan iya ba,ta kankame Shi jikinta na wata irin tsuma muryarta ta dishe tamkar me yin mura ta Fara magana. "Dan Allah ka bari wallahi marata ciwo takeyi...". Baiyi magana ba sai kakkameta da yayi kamar ze shige jikinta shima ya hade bakinsu Yanda ba Yanda za'ayi ta iya furta wata maganar ba, hannunsa ya tura Yana shafar marar ji yayi tadan tasa kamar ta Dan kumboro, hannun ta rike tana girgiza Masa Kai. Zare hannun yayi ya dawo dashi sama yaci gaba da sabgarsa ya Kuma ki sakin bakin da zatayi korafin, suna haka har wayarsa ta Fara rera kiran sallah. A hankali cikin muguwar kasala ya saki bakinta yana Maida numfashi da sauri da sauri gefe ya margina Yana dafe da tasa marar idanunsa a rufe, Zahra naji ya raba jikinsu ta Kara takurewa a cikin bargon wani irin tsoro ne ya lullube ta da gaske yazo Mata da wani lamari Mai girma, ita ai ko idanu bazata yarda su hada ba ai da kunya wallahi duk yabi ya tsorata tas ya lalube ko Ina na jikinta, Ashe can baya Wasa ne kawai yayi Mata yanzu ne ya nuna Mata true colour dinsa tana ganinsa salihi Dan bawan Allah Ashe shima guda ne ba gyale ba, kirjinta sai zogi da ciwo sukeyi mata yayi son ransa da jikinta. Tana jinsa ya tashi ya shige toilet ya jima tana jiyo motsinsa, sannan taji ya fito alamun tsayuwarsa taji a Kanta,a hankali ya saka hannu ya janye bargon kankame jikinta tayi Dan daga ita sai pant Kare Mata kallo yakeyi take yaji alwalarsa na neman warwarewa, laimar hannunsa ya Dan yarfa Mata a jikinta "wash...Allah na!". Mayar Mata bargon yayi ya shige clothset din dakin jallabiya ya sako Fara tas da hula mahadinta raka'atanul fajri yayi, jikin gadon ya matso ya Dan zauna "zanje masallaci". A dawo lafiya tayi Masa tana kudundune Yanda take, tanaji ya fice daga dakin. Sai ta tabbata ya Kai masallacin sannan ta yunkura ta tashi ta nufi toilet, tsabtace jikinta tayi sannan tayi wanka ta fito,lotion din data gani ta shafa sai body mist na itacen sandal wood Dana oud ta hada ta fesa kayan da zata saka ne ya zama cikas Dan bazata iya mayar da Wanda ta cire ba Kuma bazata Kuma Zama da towel ba tunda taga abinda hakan ya janyo Mata, Shawarar duba clothset din tayi idan taga Kaya sabo Kona waye zata saka, tana mamakin ace Mai gidan Nan bashi da Mata Kuma ya sakarwa abokai irin haka baya gudun a ring aikata fasadi a cikinsa, were Dan wannan sai ka shekara a ciki ba'asan kana nan ba. Ba karamin mamaki tayi ba ganin kayan Mata masu yawa har Sunfi na wancen apartment din ba wani d'ar undies ta saka ta saka doguwar Rigar material Bata daura Dan kwalinba wasu hulina na Mata ta gani da yawa ta duba kalar ash irin flowers din jikin material din ta saka a Kanta, barci takeji sosai Dan tunda Allah yasa ya tasheta da aalonsa Bata Kara rintsawa ba shiko gogan Allah besa an raba barcin jiya dashi ba. Harta juyo zata bar gurin taji tana son ta bude dayan side din, kayan make up ne dasu turarika shoe and bags turaren ta dauka tana dubawa duk yawanci irin nata ne sai wasu irin nasa ga Kuma kayan maza nan Lodi Lodi dasu underwears tana tsayen tana dubawa taji kawai an rungumota ta baya, ajiyar zuciya ta sauke tana lumshe ido Sam bataji alamun bude kofa ba ko takun tafiyarsa, Kansa ya Dora a kafadarta Yana Dan hura Mata iskar Bakinsa a kunne "Good morning my previous". "Morning Yayana". Ta fada da wani salo, juyo da ita yayi suna facing din juna. "Bude idonki ki kalleni ki fada min waye yayan naki? Wato har yanzu da sauran Rina a kaba kenan ko? Nifa bazaki tauyeni ba Ni ba wani Yayanki bane a bani special name Dina, kodan kinga mu 'yan gargajiya ne "ya'yan Alarammomi Malam soro, bamu da wayewa irin taku ko?" Batasan lokacin data sauke ifanunta a Kan nasa ba, tana jinjina maganarsa. "Wayewar saita kasheku". Tayi subul da baka ta fada harga Allah a zuciyar ta tayi niyyar fada bakinta ya subuce ya fada. "Kai! Nine wayewar saita kashemu to nida waye zata kashe din?" Kauda Kai tayi tana Jin kunyar maganar. *Ni ba haka nake son fada ba Bakina ne ya furta hakan". *Ok, zomu kwanta barci nakeji tunda kin hanani barci da fitinarki". Rigar ya zuge zif din ya cire mata ita ya barta daga ita sai undies kawai ya dauketa can ya nufi bed din da ita tana mutsulmutsultun ya sauketa ya kiya Saida ya dangana ta da saman bed din, shima jallabiyar ya zare ya janyota ya lullubesu da gaske barcin za'ayi Dan tunda ya sakata a jikinsa Bai Kara yi Mata komai ba. *** *** *** Tunda Ammi tayi sallah Bata Koma barci lazimi ta zauna tana yi amma zuciyar ta Babu dadi kwanan nan kusan Kullum sai tayi mafarkin Mahmud da wata yarinya budurwa Yana rike da ita da hannu Daya dayan Kuma Yana ta faman fada da wasu irin halittu mara kyawun gani, to yau ma shita Karayi Saida taga wasu mutane dattijai guda biyu sunzo sun Taya Shi kashe wadannan halittun sun tasa su shida yarinyar har wani gida sai da suka shige sannan suka juyo suka tafi. A haka Mai gidan ya sameta Saida ya zauna ya Kare Mata kallo yasan da akwai damuwa a tare da ita sai dai tana kokarin biyewa. "Ammin Yara me yake damunki duk kwanakin Nan Baki da walwala Sam ko kula dani ma tayi baya ko Baki huce bane har yanzu?". Kai ta girgiza "A'a kawai dai lamari Hussain ne yake damuna kofa da Rana Daya Bai taba kirana ba ko sako ta email Bai taba Yi min ba, gashi a kwanakin nan sai wasu irin mafarkai nakeyi dashi marasa dadi abinda yafi tsaya min a Rai Kullum da wata yarinya budurwa kamar 'yar India nake ganinsa da ita Ina tsoron wani Abu wallahi na rasa yanda zanyi Dan Allah kayi wani Abu akai". Sai hawaye sharrrr. "Subahaballahi! Haba zainab ya Zaki ringa yi Masa kuka kinsan masifar zubarwa da d'a hawaye kuwa ko wani abun yake aikatawa ai saiya karu idan kina Masa kuka, addu'a zamuci gaba da Yi Masa nifa jikina Yana bani Yana Dubai Dan last week na samu leakage akan Yana can din Dan yayi wasu ziyarorin bazata a can harya dakatar da wasu ma'aikatansa sai dai duk kokarin a gano min masaukinsa sabo hakan yaci tura Dan ba'a inda yake sauka ya sauka ba tunda gudun hijira yayi". Hawayen ta goge ta tashi tana ninke sallayar ta zauna kusa dashi. "Shikenan Allah ya shiga cikin lamarin ya kureshi daga sharrin zinace zinacen zamani wallahi badan komai nufin Allah bane Wanda yaso yake bawa kyautarsa danace dama bashi ya samu wannan budin ba da kananun shekaru to yanda yaso haka yake tsara kayansa, Amma ga yayunsa Nan ba Wanda ya takura musu Suma ai suna da wadatar,tunda Allah yayi muku karfin arziki waye talaka a cikin family din nan?". Dan murmushi general yayi Yana kallon yanda take fadin magana abinda ba halinta ba inda akan twins ne sai dai wani yayi magana Amma ta zage tana fadin son ranta. "To ya zamuyi da hukuncin Allah shi yaso ya daukaka a cikin zuri'ar da Wanda ya Isa yace a'a Ina cewa Alhaji Ishaq ne ya bashi jarin Daya Fara sana'a dasu tun Yana hannun Hajja, Amma yanzu zaki hada arzikinsu ko kusa ko alama Babu Hadi,.koni Dana haifeshi ya mallaki abinda bani da kwatqnkwacinsa, Keda Kika haifeshi kin mallaki abinda yake dashi? To kiyi istigifari ga Allah tunda shine yace Yana azurta Wanda yaso ba tare da hisabi ba,ai kin gane?". "Na gane Allah ya Zama gatansa a duk inda yake,Amma fa yarinyar Nan ta tsaya min a rai idan Yana kusa da wannan ai zai manta da kowa ne tunda cikin bacin rai yabar gida ga Kuma kudi a tare dashi kaga sai Allah kadai ze kare shi". Dariya ta bashi sai da yayi sosai kafin yace. *In Sha Allah in dai Zina gado ce to Alfarmar Manzon Allah s.a.w.w zuri'ar mu bazasuyi ba Ni ba mazunaci bane haka kema ba ita bace in Sha Allah.Allah baze jarabcemu da ita ba, Kika sani ko bushara ake Miki ke uwa kin samu sirika". "Haba dai har abun ya Kai haka yayi aure ba sanin iyayensa ai kuwa da lamarin ya lalace". 'yar dariya yayi. "Kedai kije ki shirya min breakfast daurin Aure zamuje kabba na Dan gidan sanata Abdul Aziz" "Ok.bari na shiga kitchen din" Ta tashi ta fice tana baza kamshinta as usual. ****** Tun idar da sallar Rukayya ta taso ta nufo part din da zahra ta kwana,abin mamaki an canza pin kofar dan ta kwada yafi sau goma Amma taki budewa. Nan da Nan taji hankalin ta ya tashi me Kenan badai wani bane ya shigewa 'yar mutane ba gashi jiya Taki Kai Mata wayarta da ba saita kirata ba, gudun kada tace sai sun kwana ya hata ta Kai mata. Number ya Sameer ta lalubo lokacin Yana barci, Yana dauka ko gaishe shi bata tsaya yi ba ta Fara fadin "Ya Sameer ka taimakeni wallahi tun sassafe bake kokarin shiga part din da zahra take Amma kofar kofar kamar an canza pin din na saka yafi sau goma Amma yaki budewa". Tsaki yayi "Waike Dan Allah Ruky yaushe Zaki girma ne? to oga ne ya shigo cikin dare Nima da asuba naga text message dinsa Dan haka ki Zama ready idan na shigo saimu wuce tare Amma yanzu kada kuyi komai za'a kawo abinci". "To ai su Iya Rahane har sun kusa gamawa baka fada min ba tun dazu". Ok, ba komai sai a hada tunda gidan da jama'a, yauwa zuwa an Jima ki bude musu part din Nan na kusa da parking lot sai su zauna a nan tunda shima ogan Bai san ze shigo kanon ba harsu Gama su koma to matsalar madam din ce inaga ta caza Masa Kai Wai cewa fa yayi daina amsa Masa waya tayi". "Kamar ya Bata amsa masa waya? Batasan kowaye bane da zata ringa yi masa haka?" "Eh kusan hakan ne gaskiya" "Allah ya rufa asiri" ta fada. Sukayi sallama ta kashe Kiran tana dariya "su oga anzo hannu ana walagigi da rayuwar 'yan Mata gashi kaima kazo hannun yarinya tana juyaka son ranta, nasan bana raba Daya biyu saboda shi ta rufe wayarta jiya, taki magana dashi a wayar Ya Sameer karshe ma ta sakata jirgi, yes! Haka nake son irin matansu su kasance, idan suka samu wadda ta mace a kansu ta Zama sorry Amma wannan ta shuka mulkinta yanda takeso tunda Batasan waye shi ba". Ya juya ta koma kitchen inda tabar su zilai suna aiki, tana shiga zilan tace Wai ni lafiya yarinyar Nan? naji shirun yayi yawa ko dai rakani zakiyi na gano lafiyarta kada na Zama babbar kwabo an hadoni da yarinya nayi wasarere da lamarinta". 'yar dariya. Rukayya tayi "gaskiya kinaji da matar big bro irin wannan shiga damuwa jiya fa ko barcin kirki bakiyi ba kina zaman jiranmu yau ma tun Asuba kike ta nemanta, ki kwantar da hankalin ki Aunty sirikinki ne ya taho ba Shirin wannan 'yar taki tsaye ce taki saurarensa ko a waya dole ya tsallake hidimominsa ya nufo Nigeria". Iya Rahane ce ta aje Wukar hannunta tana duban Rukayya "kikace uban gidan mu ya shigo garin?" "Kwarai kuwa iya jiya cikin dare ya shigo Kinga kuwa sai ki fadawa Aunty ta kauda Kai kawai gurin son ganin 'yarta ba yanzu ba gaskiya, Dan haka da an gama aikin Nan zamu bar Nan Bangaren mu koma wancan". "Wannan gaskiya ne inba tayi dalili ba yaushe zamu shigo wannan guri harda kwana a cikinsa, Amma dalilin uwar dakinmu mun dangwali arziki ai wannan ba komai bane akan gidan da aka sauke mu a sokoto, Kai Naga inda arziki ya amsa sunansa wannan yaro uwarsa tayi farar haihuwa wallahi Nan kusa Banga mutane masu karamcin su ba, uwarsa yarinya karama sai halin girma". Ita dai zilai sai ta rasa Wai wannan maganar dawa ake ne waye suke zance a kansa ne ita fa maganar Zahra take musu su Kuma sun kamo wata tashar Ina hadin zahra ba Wanda suke magana a kansa ko dai Mai gidan ne ya dawo Basu gane me take nufi ba, ita Zahra matar Almajirin Malam Bukar Wanda gidan zaman ma na Baba Malam ne mutanen da yaje yiwa aiki turawa suka gyara Masa shi, to Ina shi Ina wannan Aljqnnar duniyar suda aka kawosu zaman 'yan kwanaki na ganin likita. Cikin nuna mamaki zilan tace "ikon Allah ai ban sani ba kice da anyi uwar banza gara da Kika fada min kada naje nakai kaina girma ta Fadi". "Ai Koda kin shiga basa Nan ba a nan suka kwana ba". Wayar Rukayya ce tayi qara ta dauka ta fice daga kitchen din shine abinda ya Hana zilai fadar abinda tayi niyyar tambayarki Rukayyar. Hira iya rahane taci gaba da yiwa zilai a Kan Mahmud amma ko Daya zilan Bata gano ainishin waye take magana a kansa ba. .