Follow this link to join my WhatsApp group: https://chat.whatsapp.com/JA5Ut6Au0j3DAjud3Ih37Q *Z A K I* By Khadeeja Candy 1️⃣ Carar Zakaran dake harabar gidan ne ya katse min dogon bachin da nake. A hankali na matsa fuskata dauke da murmushi domin ko kadan hakan be bata min rai ba, na daga hannuna a sama ina mika tare da kara watsakewa, kamar kullum yau ma bachin ya min dadi, ba dan gurin da nake kwanciyar ba, sai dan farinciki da kwanciyar hankali da natsuwa irin ta masu wadatar zuci data cika min zuciyata nake kwanciya da ita a kowane dare. Kamar wacce akai wa dole haka na bude manyan kuma lussasun idanuwana da suka rine suka sauya kala sakamakon dadewar da nai ina bachin. Akan farinciki na sauke idonuwana wato mahaifiyata wacce ke sanye da wani jan yade kodadden irin na talakawa kuma na gadonmu. "Wainar ki ce take ci tun dazun aka aje miki" Da yaren buzanci mahaifiyata take muna min kyanwar dake kusada ni tana cin waina. Murmushi nai na kai hannuna na shafa kyanwar kana na shiga mata magana da yaren buranci. "Kin cinye min waina ko?" "Ataa yau ba za ki je baranki ba ne?" Kanane ya tambaya, hakan yasa ni saurin tashi daga kwancen da nake, na fito daga cikin bunkar ina hamma ba tare dana rufe bakina ba, ba dan kuma ban san babu kyau ba, sai dan rashin kula da watsi da addini irin na mu na... Da hanzari na nufi wani dan guri da muka killace da kwano domin yin wanka ko kuma ba haya. Ba wanka nai ba domin wanka be dame ni ba duk kuwa da kasancewar na fi kowa tsabta a cikin gidan mu amman a hakan sai na kwana uku ban yi wanka ba. Fitsari kawai nai na fito da sauri na wanke fuskata da fassashiyar butarmu marar murfi, sai da na gama wanke fuskar sannan na nufi gurin da muke girki na dauki gawayin kara na saka a bakina na tauna na saka yatsana na wanke bakin na kuskure sannan na wanke kafafuwana na nufo bukkarmu da sauri tuna ban yi sallah ba yasa na dawo na dauki butar nai alwala na sake kowa bukkar wanda zan iya kiransa da dakinmu. Zanen dake daure a kirjina na cire na dauki riga da wando na wani shudin yadi mai kamar laile na saka na dauki hijab na saka nai sallah mai kamar asha ruwan tsuntsaye, wato da sauri domin cikin kannanen lokaci na yi na gama. Bakin dankwali na dauka na cire hijab din kaina na saka bakin dankwalin mai kama da karamin gyale na rufe kaina kamar yadda na saba ko kuma na ce muka saba. Na kai hannu na dauko madubi tare da gawayin dana daka na kwaba tare da man shafi a guri daya, tsayawa nai kallon kaina a madubin ina murmushin daya kara bayyanar da kyauwona har dimple dina suka bayyana, sai faman lumshen manyan idanuwana nake ina budewa. Abu ne da ya ke bayyane, bana bukatar kowa ya kalleni ya fada min cewar ina da kyau, kyau na hali ko na halitta kyau na jiki ko na fuska, ni kaina idan na kalli madubi kyawona tsorata ni yake, idan ba a kirani balaraba ba to ba za a cireni a jinsin india ba indiyawan ma sai an tona, hakika ni kaina na san ina da kyau na wuce misali, kyan dake hana ni shakaf a cikin al'umma, gashin kaina kadai idan na sake ya sauko mutune har mamakin yadda nake da yawan da tsohon gashin dake saukona har mazaunaina suke. Ba sai na fada ba, duk wanda yasan jajayen buzaye yasan su da kyau da gashi sai dai a cikinsu ni din ma ta dabam ce a bangaren kyau. Man dake gabana na gawayi na dauka na shafa a fuskata a take farin fuskarta da kyau ya gushe na koma kamar ba ni ba, dogon hancina kawai zaka gani ka iya gane ni shima kuma sai idan ka sanni farin sani sosai. Sannan na mike tsaye na dauki kwagirin dana saba ratayawa a koguna (kwankwaso) idan zanje yawon bara na daura. Gurin da mahaifiyata take zaune naje ina mata sallama da yaren buzanci. "Na tafi Nana" Haka nake kiranta da sunan dana tashi naji mutane na kiranta da shi duk kuwa da kasancewar ba shine aihanin sunanta na gaske ba. "Allah ya tsare a samo da yawa" Ta fada min tana dariya ni kuma na kada kai na fice ina murmushin domin bata san gaskiyar abun ba, a duk tsawon kwanakin da nai ina aikin. Sai da nai nisa da bukkarmu ta yadda babu wanda zai iya hango ni sannan na ra6a ta cikin kangon gidan da muke gaban bukkar mu wanda wani shahararren mai kudi yake ginawa na shiga ta gurin da aka fasa domin yin windows na fada cikin wani gurin da ban san me za ayi da shi ba, daki ko falo, na dauki kayan aikina na bi ta kofar gaba na fice, na saba ba tun yau ba, idan nai nisa da gidan mu da sunan zuwa bara kamar yadda mahaifiyata take saka ni sai na biyo ta window kangon gidan na dauki kayan wankin motana, na bi ta kofar fita na fito, har yau mahaifiyata bata ta6a sanin cewar ina wannan aikin ba, ni kuma ban ta6a ganganci fada mata ba, domin na san zata hana ni idan ta gano ba bara na ke ba, kamar yadda take son nai, ni kuma bana son barar domin tana ci min rai, kamar yadda take kankantar ni ga duk wanda na mikewa hannu na ce ya bani. Ya zame mana kamar al'adar yin bara a titi ko manyan gidaje ko ma'aikatu domin samun abunda zamu ci, wasun mu suna da shi wasunmu suna da rufin asirin da zasu iya rike kansu ba tare da sunyi bara ba, tsabanin mu da kullum sai mun yi bara muke samun abunda zamu ci. Na sha ganin irin wulakancin da ake ma mahaifiyata kala kala idan muje bara musamman akan titin manyan motoci wanda hakan yake bakanta min rai, sai dai ita ko a jikinta duk kuwa da irin kyamar da ake nuna mana. Wannan dalilin ne yasa na daukar mata alkawarin cewar zan rika yin bara da kaina ina kawo mata kudi ita ba sai taje ba, da wannan ta dogara ni kuma na sauya hanyar bara zuwa neman na kai, duk kuwa da kasancewar wasu na min dariya ganin kamar aikin be dace da ni ba, wai ace mace kamar ni ina tsayawa a inda motoci ke tsayawa saboda traffic ina wanke gilashin mota ana biyana, aikin da akasan maza ne suke yi. Nikam hakan be taba damuna ba, domin na san yafiye min bara kuma ina samun sosai fiye da baran ma, ganin ni macece yasa wasu mazan ba hansin suke ba ni ko ashirin ba, har dubu daya na kanyi dacen wani ya bani. Ba dan kuma an san ni din wacece ba, domin kullum fuskata shafe take da fantin gawayi wanda hakan kan jama min kyama a gurin wasu, sai dai ni yafi min kwanciyar hankali na boye kyauna na, gudun abunda zai iya biyowa baya, za a iya kawo min hari kamar yadda aka sha min lokacin da muke wacan gidan da ba a tashe mu ba, duk wanda ya kalle ni a aihinin yadda Allah ya hallicce ni ba za a min kallo daya a dauke ido ba, ba kuma za a ki fadar cewar ina da kyau mai jan hankali ba, mata ma sukan fada balle mazan da babu adadi. Ko a unguwar da muke zaune a yanzu wato Clapperto babu wanda ya san iya ainahin yadda fuskata take, domin kullum ina tare da bakin gawayi a fuskata, wanda hakan kan sa a kara kiranmu da kazamai, ganin irin gurin da muke zaune mai kama da juji, wani kangon fili ne kato wanda aka ware wani bangare na filin aka fara ginin gida kuma aka bari, lokacin da aka tayar da mu daga wacan kangon gidan da muke rabe sai muka dawo wannan muka zauna ba tare da tambayar izinin mai shi ba, muka kafa yar bukkarmu muka zauna a nan muke rayuwarmu ta yau da kullum. Na saba tafiyar kasa, dan haka komai nisan guri ni baya damuna, ina tafe ina rare wakar mu ta buzanci wance mahaifiyarmu take yawan rarewa a gida, idan na dora alkalamina a ko wane kalar littafi zan cika shine da kalmar kaunar iyalina kamin na bayyana komai na rayuwata, ina son yan uwana kuma ina son yarena da al'adata fiye da komai a duniyar nan. A sannu nake tafiyata har na iso babbar flyover din Alu inda na saba wanke motoci ana biyana, kamar kullum mutane suna ta kai kawo a gurin kama daga masu babura da masu napep da kuma masu motoci manya da kanana. A cikin a kusa na soma sana'ata idan naga babu motoci sai na koma inda muke zama ni da abokanin sana'ata yara maza mu zauna sai idan an sake hada motoci sai muje da gudu mu wanke wasu kuma suna siyar da popcorn wasu kuma pure water, wasu air freshener da turare dai sauransu. Sai da yamma lis na nufo gida gani a gajiye amman ba zan iya cire kudi na hau abun hawa ba, a ganina idan na hau kudin zasu ragu, kamar yadda mahaifiyata ta koya tun a lokacin da muke bara. A hanya na siye pure water da gyada ina tafiya ina ci can ta tsallaken titi nake hangon wasu buzayen irina a jikin wata motar suna mika masa hannu ya basu, ni dai ban da kallonsu babu abunda na ke, ban ankara ba naji an watso min ruwan saman da akai kwana biyu da suka wuce, wadanda suke kwance a gefen titin sakamakon wucewar da wata motar tai da gudu kamar zata tashi sama. Wani bakin haushi naji domin ba kadan ruwan da motar ta taka suka bata min tufafi ba da kuma kayan aikina, dan brush da man wanke mota da kuma kyalena na gogewa idan na wanke. Bance komai ba naja tsaki na cigaba da tafiyata, yo daman wa zance wa wani abu tunda ni kadai nake ta tafiya ta. A natse nake tafiya ta har na karyo kwanar dana saba bi idan zanzo gida, ina yanke hanya ne domin abun ya zo min da sauki, sai dai duk da haka ana kiran magariba na soma dosowa unguwarmu ta Clapperto road, a dai dai bakin gate din gidan dan Uti idanuwana sukai arba da kalar motar da wuce ta gabana dazun ta bata min tufafi, kuma wani abun dadi babu mutane a titi sai karar motocin dake kai da kawo. Sai da naje gaban motar na leka gaba babu kowa a ciki, sannan na kara matsawa ina kara tabbatarwa idan ita dince ko aa, kalar dai daya ce sabuntar ma daya ce sai dai wannan anyi mata hoton ZAKI a jikin number motar kuma an rubuta mata ZAKI 001 da manyan haruffa tsabanin wacan da ban kula da number motar ba ma balle ma na san me aka rubuta. Komawa nai ta inda na fito ina ta kalle kalle har na hango wani katon dutse da be fi karfina ba, na dauko na zo na jefawa motar ta gurin gilashinta, a take ta fara kuka, ni kuma na ranta cikin na kare, ai daman dai burina na dauki fansa, ko ba shine ya bata min tufafi ba be dame ni ba dan dan'uwansa ne mai kudi sai suji yadda ake ji... Abunka da marar jiki nan da nan na karya kwana kwana ina ta sauri kamar an biyoni, tsoro ya saka na kasa mikewa kai tsaye na bi titi na isa gida, sai na shiga ta hanyar gidan taba (Gidan azaba) na bulla ta can kwantagora road na karyo ta wata hanyar, domin kawai wahala sannan na bullo da gidajen yan sanda da yake nan na biyo ta bayan gidan Alkali Abu dange wato gidansu Khadeeja Candy na fito titi Clapperto road na doshi gidanmu. A inda na saba aje kayana na nufa na aje sannan na fito ina kirga kudin dake jakata, kamar ance na waigo ko da na juyo sai na hango wata halitta mai kyau da daukar hankali da kuma ban tsoro tana kallona. Mutum nake hange amman a siffa da fuskarsa, sai dai kwarjininsa da aibarsa kamar wani zaki. Nesa yake da ni amman fuskarsa zooming take min tana kawo min shi kusa kamar yana tsaye a gabana. Annuri ne shimfide a fuskarsa, sai dai ba irin na masu dariya da sakin fuska ba, irin wanda annurin ya zame masa jiki yake bayyana kansa a duk lokacin da mai shi ya kalleka, kwarjinsa ya cika min ido har kure ganina nake ganin kamar daga ni sai ainahin Zakin ne a jeji, wani abu mai zafi naji yana bin kafafunawa, ashe fitsari nake a tsaye ban sani ba, tsabar tsoro ya cika min ciki sai na fadi zaune a gurin na rufe idona kunya ce ta kamani budurwa kamar ni ace tai fitsari sai kuma naji ashe ba kunya ba ce tsoro ne..... __________________ Who's ready for the next chapter? #ZAKI #Vote #Share #Comment. Thanks Share Pls🙏🏻 *Z A K I* By Khadeeja Candy 2️⃣ Mafarin ko wace Rayuwa numfashi da jini ne, ne numfashin da nake fitarwa ne ya tabbatar da cewar a raye na ke. Sai dai bana iya tantance yadda nawa numfashin yake a yanzu, domin surkinsa da wani kalar iska ne mai dadi shaka. A take na bude idona sai na hango gurin da mutumen yake tsaye kamar anyi ruwa an dauke domin babu alamarsa balle shi din yayi batan dabo bat kamar be taba wanduwa a gurin ba. Wata kila yaji tsoron fuska ta ne dake da bakin gawayi ko kuma rufen idon da nai ya tsorta shi, shiya saka yai hanzarin barin gurin. Samun kaina nai da murmushin kaina saboda tsoron dana ji, na Lumashe ido ina shakar kamshin turare mai shiga har cikin kwakwalwa ya samawarda natsuwa ga marar ita ga mai ita kuma ya dada masa. Na risina na dauke kudina da suka zube ina dariyar kaina, domin sai a yanzu abunda nai yake bani dariya na fashe gilashin motar mutane saboda mai motar ya watsa min ruwan kazanta a jiki, wata kila ma ba shi yai ba. Lokacin dana hango mahaifiyata tana a gaban murhu sai farinciki da jindadi ya lullube ni, domin ba kasafai zaka zo ka tarar an dora girki a gidanmu ba, mun fi siyen garin kwaki mu jika ko muyi kwado (Datu) da kuli mu ci, idan wadatar tai mana yawa muna siyen kanzon tuwon dawa ko na shimkafa mu aje muna ci, hakan yasa na iya sarrafashi ta ko wace siga, idan nai jalof dinsa sam ba zaka ci ka dauka cewar kanzo ka ci ba har sai idan na fada. Ban saba shiga gidanmu da sallama ba, dan haka yin sallamar be dame ni ba sai kawai na karasa gurin mahaifiyata ya kai hannu na bude tukunyar dake kan wuta ina fadin. “Nana me kike dafawa” Ba shiri ya yada murfin sakamakon wani azababen zafi da naji a take yan yatsuna sukai ja, sai dai ganin taliya yasa ni manta zafin dana ji duk kuwa da irin halina na raki sai wani farincikin ya kara baibayeni har na hade yawu. Ina son taliya sosai musamman dafuwar masu kudi ba irin tamu ba da sai an sauke muke saka yaji da magi wani lokacin ka gishiri kawai za mu saka mu ci. “Taliya ce nake dafawa” Ta bani amsa itama fuskarta dauke da far'a. “Ina kuka samu kudi?” “Bayan fitarki Maman Maryam ta aiko mana da ita” Na yi dariya ina saka hannuna a kwagirina dake kuguna na ciro duk kudin da nai na mika mata, ban san na rage ba balle har na cire wani abu ko da kuwa ina da bukatar siyen wani abu ne, har sai idan Nana ta dauka da kanta ta bani. Gaba daya kudin da nai a yau ba su wuce dari uku da yan canji ba, daman ba ko wace rana ce jumma'a ba. “Wai Ataa ina kake zuwa baran ne? Kullum kudin da kake samowa be wuce wanda za si abinci da safe ba, da rana haka muke wuni babu komi a ciki inda ba Allah ya kawo mana wani abun ba” Na yi shiru domin ban san me zan fada mata ba, tana da gaskiya a lokacin da take baran tana tara kudi mai yawa har ma ta siye wani abun ta aje, tsabanin yanzu dana hanata kuma ni bana iya kawo abun kwarai domin ni ba baran na ke ba. “Nana kin san ni ban iya baran sosai ba, kuma bana son zuwa gurin manyan motoci ba” “Ka gani Ataa ka cire wannan girman kan, ka raba kanka da girma kai ka ba dan kowa ba, idan za ka dage ka yi bara ka dage domin shi ne komai na mu” Fada take min amman dariya nake, saboda yadda take kirana namiji kamar yadda take yi ma ko wace mace idan kuma namijin ne sai ta mayarda shi mace, domin ita har yanzu hausarta bata gama fita ba. Sai itama tai dariya domin ta san abunda nake yi ma dariya. Daga haka na samu na shashantar da maganar na tashi na dauki fassashiyar butar mu na zagaya a inda muka killace na wanke fitsari sannan na fito na saka sabulu na wanke fuskata mai bakin gawayi nai alwala na shiga bukkarmu. Ban samu kanena Lukman a bukkar ba hakan ya tabbatar min da cewar yana islamiya kenan. Iyakar kokarin da nai na canja tufafin jikina ne na saka wasu sannan na soma rama azahar kamin na dora da la'asar. Ba tozarci ba, ni kadaina ina shakkar sallah da muke a bukkarmu domin na taba ji a lokacin da nake zuwa makaranta ana cewa Allah baya karba sai mai tsarki sai dai ban iya banbancewa ba tsarki na fitsari da janaba ko kuwa tsarki irin wannan na tsabtace daki. Babu wanda zai iya zama dakin mu yai minti biyar a ciki saboda zarnin fitsarin Lukma da kuma na kayan daudar da suke bukkarmu ga tarin kwanoni marasa marafe da kuma tarin gwangwayen da Nana take tarawa wai idan suka kai buhu uku zata siyar. Ina sallamewa kunnuwana suka sato min muryar Lukma dake fadin. “Nana kin dawo gurin baran?” Juyo nai da sauri ina kallonsu daga inda nake zaune, daga ita har kanena basu san ina yi ba. “Nana bara kike zuwa?” “Ataa idan be je bara ba, da me zan dafa taliyar nan?” Daga can gaban murhun ta amsa min kai tsaye. Wani abu na ji ya tsaya a kirji wanda ya saba tsaya min a duk lokacin da mahaifiyata taje bara. “Amman Nana na fada miki zan rika yi ba” “Ba inda kake zuwa kake zuwa (Nake) kai wani guri kake tafiya dabam” Na turo baki baki ina bata fuska. Har tai girkin ta gama ni fushi nake ta yi dan taje bara sai dai hakan be hana ni cin taliyarba, sai dai ni sai da naje na siyo man kuli na zuba sama da yaji sannan abun ka da mai kwadayi baki baya son ba dadi. Washe gari ma kamar ko wace rana sai da haske rana ya leko bukkarmu sannan na farka daga bachi, a maimakon na tashi sai na kara dunkulewa cikin wani tsohon zanen gado wanda rabinsa ya gama yagewa (Barkewa). Bana jin yau zan tafi aikin dana saba zuwa da sunan bara, inda har zan je nai abunda zai kare mutumcin mahaifiyata ita kuma ta zaga baya idona taje bara banga amfanin zuwan nawa ba. Dan haka ban fito daga bukkarmu ba sai kusan tara da rabi duk da kasancewar babu agogo a bukkar balle na iya ganewa sai dai a yadda na auna tara tayi ko ma ta dan gota. A lokacin ne na dauki butarmu na zagaya can nesa da bukkarmu a wani fili da aka ware ban san me za ayi da shi ba, a nan na saba yin ba haya ta a duk lokacin da bukatar hakan ta kamani, domin a wacan gurin da muka zagaye da kwano da sunan bandaki idan mukai ba haya a ciki sai mun kwashe mun kai can nesa mu zubar a kullum ni kuwa zubarwa ne yake bata min rai, na zabi nai nesa da bukkarmu nayi bahayar a inda aka tana da domin yin wani abu. Bayan na gama na dawo na saka kasa na wanke hannuna sannan na saka sabulu, sai kuma na dora da alwala sannan na shigo dakin nai sallah asuba. Da yaren buzanci mahaifiyata ta fada min cewar na dauki waina mai kuli na ci na tashi muje bara. “Ni bana son zuwa bara Nana” “Sai ka je, gaba daya zamu je” Haka na turo baki na bata fuska sosai kamar zanyi kuka, amman hakan be saka ta kyaleni ba, har sai da na ci wainar ina ta fushi daya kasa boye kyawon fuskata, har sai ta na dauki bakin gawayi da mai na shafe fuskata da shi sai gani na fito wata mummuna kamar ba ni ba. “Kin fi son ki shafa bakin gawayi kullum a fuskarki kamar wata dodo” Mahaifiyata ta fada da yaren buzanci, daman can tafi kowa tsarguwa da shafa gawayin da nake domin yafi min kwanciyar hankali da lamana. Ko ba komai hakan hana sa ana min kallon kazama wanda ba karamin kariya yake min ba, na san da ace yan iskan mazan da suke unguwar za su ga ainahin yadda fuskata take wata kila da ace cikinsu wani ya keta min haddi.... Cikin rashin maida hankali na saka tufafin jiya masu kama da farin lela na yafa bakin gyale kamar yadda yawancin buzaye suke yi, mahaifiyata kuma ta yafa fari wanda ya gama dafewa ya canja kala saboda tsufa da kuma lalacewa. Lukman ya dauka yar robar ruwansa da kuma ta bara kamar yadda ya saba Nana kuma ta dauki ghana must go dinta ni kuma na daura jakata (kwajiri) a kuguna sannan na dauko wani tsohon gidan sauro ya rufe a saman bukkarmu a daidai inda kofar dakinmu kana na dauko wano (Langalanga) na rufa a gurin kofar kamar yadda muka saba idan za mu fita unguwa. Nana na gaba ita da Lukman suna firarsu abun shawa'a ni kuma ina baya ina kallonsu har muka isa gaban manyan shagunan da suke gawon nama inda manyan motocin masu kudi suke tsayawa siyen abu. Kamar yadda muka saba a can baya lokacin da muke baran ni nakan tafi gurin wata motar dabam Nana kuma ta tafi gurin wata dabam ita da Lukman idan mun fita tare da shi, idan kuma gida muka bar shi to ni da ita a tare zamu rika bin motoci ko kuma mutanen dake shiga cikin shagunan. Ba ma magana sai dai mu muka hannu mu marairaice fuska kamar za mu kuka ta yadda mai ba mu zai dauka ba mu da sama balle kasa ya taimaka mana. Haka muka wuni a gurin muna ta mikawa mutane hannunmu idan ya fito daga mota ko zai shiga wani shago har muka tara da dan yawa, duk abunda mahaifiyata ta siya sai ta aiko Lukman ya kawo min na ci. A haka muke har yamma tai daf da zamu tafi gida na hango wata motar a fake da sauri na nufi motar a zatona akwai mutane ciki sai da na isa sai naga babu kowa a ciki sai dai gilashin motar a sauke yake. Ina juyowa sai naji na bugu mutum, da sauri na dago kai sama ina kallon wanda na buga din, dogo ne mai faffadan kirji mai tsananin fari ga kwarjini da haifa, duniyar kamshinsa ta tunatar da ni cewar shine dai mutumen dana fasawa mota a yanzu ma ji nai na zama wata yar tsuntsuwa, yana ta kallona da fuskarsa mai dauke da walwala kuma ba walwalar ba, ba kuma ra a kira shi da rashin walwala ba, amana dai ba yabo ba fallasa a bayyana yake kana kallonsa kasan abu ne mai hawayin ya dabbata Sunnar murmushi a addininsa. Kwalla nake saboda ainahim zatin fuskarsa da nake kallo, ba hawayen kyawonsa ne ba, ba kuma na rashin far'ar fuskarsa ne ba, na tsoro ne irin wacan tsoron daya kamani jiya a lokacin dana hangoshi tsaye yana kallona, banbancin wacan karon da wannan a jiya fitsari nai yau kuma kwalla ne a idona na tsoro da fargabar abunda zai min. Lokaci daya naji an fisgoni wanda hakan ya bani damar sauke numfashin da ban san ina rike da shi ba sai a yanzu. “Yana son ya shiga motarsa kin tare nasa hanya Ataa” Nana ta fada tana rike da hannuna, ji nai na dawo duniyar mutane mai cike da hancin iska. Da hanzari mutumen yai saurin cire jacket din jikinsa ya bar t-shirt saboda na dan shafe shi kadan lokacin da mahaifiyata ta janyo ji domin na bar jikin motarsa, cike da kyankyami ya bude boot ya saka jacket din ya rufe ya dawo mazaunin gaba ya zauna yana goge hannunsa da tissue paper saboda ya rika rigar dana shafi gefenta kadan. Sai a yanzu na gane, wato duk tsayin da yake yana kallona na jiran na bashi guri ya shiga motarsa ne, amman ba zai iya yi min magana ba, wata kila maganar wahala take masa ko kuma yana kyamar furta kalmar kauce na shiga motata ga mace iri na ne.... Ni dai da kallo na bi motar sai a yanzu na lura da number motar ita ma ZAKI ne rubuce a jikinta, sai dai wannan motar ba irin wacan bace ko a kala balle a kama. “Miya saki kuka?” Na na ta tambaya da yaren buzanci tana nuna hawayen fuskarta. Sai na saka hannu na share na bata amsa da hausa ina turo baki kamar wata shagwa6a66iya. “Tsoro na ji” Dariya tai Lukma ma yai min dariya ni kuma na kara turo bakin kamar zan cireshi gaba daya... Sai da aka fara kiran sallah sannan muka dawo gida, a yau ma yar kullum ce sai da na wanke fuskata sannan na rama sallar da ake bina kana nai sauran, Mahaifiyata akam ba a magana domin sallah bata dame ta bayan sallah asuba bana jin tana wata Sallah sai idan ta kama. Lukman Nana ta aika ya siyo mana gari da sugar muka jika muka sha, ni kuma na roki Nana naira hansin a kudin dana samo ta bani na siyama kyanwata kifi na bata, tana ci ina shafata ina murmushi ina sonta sosai domin Allah ya saka min son kyanwa musamman wannan da muka sabu wani lokacin har fita nake da ita idan zan je wani gurin. Washe gari ma haka na farka raina fes zuciyata kal kamar yadda na saba farka a ko wace safiya ta Allah duk kuwa da irin rashin da muke da shi. Sai dai yau ta sha banban, dan kekasa kasa nai na ki yarda na bi mahaifiyata da taga bana son zuwa sai ta kyaleni a bisa sharadin zan je inda na saba yi nai ba tare da ita ba. Bayan ta fita nima na shirya na shiga kangon gidan nan na dauki kayan aikina na kama hanyar Flyover din Alu. Ina isa na fara aikina na wanki mota a biyani, idan na hango manyan motoci na fi saurin zuwa na wanke musu domin sun fi baka kudi tsabanin na direbobi da wasu sai dai su wuce su barka ma ba tare da sun baka komai ba, wasu kuma su samma maka abunda ya samu. Wata fara mota mai bakin gilashi na zubawa mai na fesa mata ruwa ina gogewa kamin traffic ya sakesu, bayan na gama na dawo ta gaban gilashin motar ina jiran mai ita ya sauke gilashin ya bani wani abu, A hankali aka zuke gulashin motar sai fuskar mutumen nan na jiya da shekaranjiya ta bayyana, a maimaikon ya bani kudina sai ya miko naga an zuro min hannu. “Ba ni wayar da kika sata?” Hannun na mace ne haka zalika muryar ma ta mace ce, sa tsakanin ba ni wayar da kika sata da kallonsa fuskarka da nake sai na rasa wane yafi wani razanar da ni, duk kuwa da kasancewar ba ni yake kallo dan da alama ni din ma ban isashe shi kallo ba, traffic kawai yake jiran a sake ya ja motarsa... ____________________________ Yaushe Ataa ta saci waya kuma? Wanene wannan mutumen? Ya dandanon labarin yake a kwakwalwarku? Akwai suga kuwa? 😃 #Vote #Comment #Share #Zaki https://my.w.tt/GuQH5GZKb9 *Z A K I* By Khadeeja Candy 3️⃣ ALIYU POV.   Ana sakin traffic din yaja motarsa sukai gaba. Husna ta waiga tana hango Ataa wacce ta koma gafen titi tana hango motarsu tana jin kamar ta koma amman ba dama. “Wannan ya zama na karshe i mean na last last time da sauke gilashin motata ki yi magana da wani saitin kunnena” Ya fada ba tare da ya kalleta ba, tsif tai kamar babu ita a gurin, ta san halin Aliyu sarai dan haka bata sake yunkurin sake yin wata maganar ba har suka isa bakin gate din gidasu. Bata jiran ya ce ta fita ta shiga gida, tasan halinsa farin sani ba tana da wahala ya iya bude baki yai magana musamman a inda zai iya isarda sakonsa da ido. Bude motar tai ta fita shi kuma ya hau titi ya dauki hanyar gidansa.    Horn daya yai aka bude mai gadin ya bude masa gate da sauri sanin cewar baya son jira, yayi minti biyar a cikin motar sannan ya fito yana rike da wayarsa ya nufi wata katuwar kofar mai ruwan zaiba. Door bell ya danna, Rahama ta bude masa kofa duk ta wani hade rai, kallonta yai from head to toe wani farin yadi ne a jikinta mai tsarin ja yadi ya fito da kyaunta da kuma dark skin dinta. Murmushi ya sakar mata kadan a maimakon ya fada mata cewar tayi kyau, sai ya ratsa gefenta ya shiga cikin falon kai tsaye sama ya haye ya shiga dakinsa dake cike da kamshin turare. “Ni fa ba zan iya ba, na fada maka na gaji gaji” Rahama ta fada bayan ta turo kofar dakinsa ta shigo, zuwa tai kusa da shi ta tana da yi masa mitar data saba. “Aliyu na fada maka ni gaji, ga zafi sokoto ga wannan uban aikin fisabilillahi baka min adalci, baka tausayi na, tun farko sai da na fada maka ni ba zan iya zuwa na zauna ni kadai ba kace za a samu mafita gashi nan ka barni kullum sai sai wahala na ke ta yi” Be dago ya kalleta ba, har ya gama cire agogon hannunsa ya bude maballan rigarsa sannan ya juyo ya rika kanta ya sumbanci goshinta ya saketa ya nufi bathroom. Ta saba inda fada ne zata yi ta gama be ce mata uffan ba wani lokacin ma har tambayar yake shikenan ko akwai wani? Magana tana masa wahala ainun kamar wanda aka idan yai maganar zata ragu .Haka rayuwarsa take tun yana karami indai ka girmeshi yai maka laifi sai dai kai ta nasa fada ka gaji ka bari ba zai ce uffan ba, idan kuma shi ne a sama da kai to baka isa ka daga kai ka kalleshi ba ma balle har kace zaka masa fada. Baya son yanayi, magana tana masa wahala ko da zo ki karba ne, baya jira sai dai a jira shi, yawan kallo yana bata masa rai ko da kuwa shi zai shafe sa a daya yana kallonka ne, baya son hayaniya and when ever he say no that's means no for sure. Duk wanda yake masa da shi a cikin familynsu tun daga dangin uwa har na uba babu wanda ya isa ya tsare Aliyu da kallo balle kuma har ya cilasta shi yin wani abu. Mommy ce kawai ta isa da shi sai Daddy bayan su babu mai kallon idonsa kai tsaye yai masa umarni da yi ko hani. Wanka yai ya fito daure ya tawul fuskarsa kamar ko yaushe ma'ana babu far'a balle murmushi. Kamar be san da zaman Rahama a dakin ba haka yabi ta gabanta ya wuce zuwa gaban maduba yana shafe jikinsa da karamin tawul. Tsadadden man shafi mai kamshin gaske ya shafawa kansa sannan ya juyo ya nufi wani bangare na daki da aka ware aka zuba masa tufafinsa a ciki. Rahama ta biyoshi tana magana cikin bacin rai. “Ni fa na fada maka na gaji” Be ce uffan ba, kuma be bar mata wata alama da ke nuna cewar yaji abunda take fada ba, ba kuma dan be ji ba sai dan haka dabi'arsa. A gabanta ya kwance tawul din jikinsa ya shirya cikin wasu kananan kaya wadanda suka kara fitar da kyaunsa da kuma aibarsa fuskarsa sai annuri take kamar sabon ango. Wata yar karamar dorowa ya janyo ya dauko pen da memo aurensu yai rubutu a kai ya mika mata sannan ya fice daga gurin zuwa bedroom. “Na yi Magana da Mommy tace za a samo aikin, amman tace ki daina wahala da yawa saboda ciwonki kuma Jawahir zata rika zuwa tana rika miki aikin gida” Tana gama karantawa ta saki paper a nan, ta saba karanta abunda baya iya fada mata idan an maganar basa kusa, wani lokacin kuma sai ya zauna ha fada mata kamar ba shi ba. Yana gaban madubi yana fesa turare ya hangota ta fito sai ta jingina da kofar closet din tsa dayan hannunta ta rike kanta, da sauri ya aje turaren ya nufi inda take hankalinsa a tashe ya rikata ya dawo da ita jikinsa daga jikin kofar closet din. “Kin cika yawan magana Dear, kuma kinsan matsalarki” Ya fada yana kissing front head dinta. “Na yi magana da Doc Asim yace za a samo very soon, idan an samu sai muje waje a dasa miki, i can't wait to see you alive healthy” Ya rumgume tsantsan a kirjinsa yana shafa bayanta kamar ba shi ba. ATAA POV. Sai da na kalleshi da kyau sai na gano ba shi yake min maganar ba, wata ce mace ce mai kama da shi take maganar   tare da ziro min hannunta mai kunshin lallen hausa wanda yai baki sosai a farin hannunta. Ba tsaya karbar kudin wankin motar ba domin gaba daya hankalina ya gama tashi sai na juya da sauri na koma can gefen titi na tsaya ina kallonsu, jira nake naga ko zai fito ya biyo ni amman sai naga be ko kalli inda nake ba, yarinyar ce kawai ki aiko min da sakon zagin da hannunta. Wutar traffic ta saki suka kama hanya shi da sauran mutanen da ke tsaye da motocinsu, sannan na soma tambayar kaina, wai wayar waya na sata? Yaushe nai satar? A ina nai satar? Na san muna da talauci da yunwa amman hakan be tana saka mu maida abun wani namu ba, yo ni ina ma naga wayar balle na dauka. Wata kila wata mai kama da ni ce tai satar to amman wayar waye aka sace a cikinsu? Ita ko shi? Idan tashi ce ai da shi zai yi magana ba ita ba, ita kuma ai ban tana ganinta ba balle har tace na mata sata ko dai shine yai min kazafi yace na masa satar?   Koma dai mienene zan yi iya kokarin da zan yi na ga ban sake ganin wannan hadaddiyar fuskar tasa ba, wacce bata ko kallon mutane da kima balle har ta martabasu, yau kwana uku kenan kullum idan na hadu dashi sai wani abu marar kyau ya faru da ni, da farko fitsari nai kuma ya watsa min ruwan kazanta, na biyu kuma kuka nai har da wani jefar da rigar dana taba shi sai ka ce ni din ba mutum ba ce, wannan karon kuma an laka min satar wayar da ban san kalar ba. Har nai na gama na nufo hanyar gida babu abunda nake sai miti da surutun rashin alherin da yake tare da wacan mutumen iyakar alkawarin da na daukarwa kaina ba zan sake hadu da shi ba, da alama nan gaba cewa zai yi wani na kashe ko kuma ya takani da mota ya wuce. Yau kam ban dawo da wuri ba, domin a hanya magariba tai min, hango manyan motoci guda biyu a gidan da zan iya kiransa da hamu yasa ni hanzarin cira kafa na karasa ciki da sauri, Nana na samu risine a kasa tana rokon wani mutum kamar zata fasa kuka. “Dan Allah ke yi hakuri Wallahi babu inda zai je, shiyasa ya laba nan shi da yaranshi” Babban mutumen mai rigar arkin dake nuna isarsa da tarin dukiyarsa ta dakawa Nana tsawar da har sai da naji ciki raina. “Babu ruwana da wannan, akan mi za ku zo ku bata min gida, ku san nawa na zuba na siye filin nan, an fara min gini sai kawai ku zo ki shige kuna lalata min guri” A nan nima na zubar da kayana na shiga rokonsa kamar yadda Nana ta hade hannayenta tana rokonsa. “Baba dan Allah kai hakuri Wallahi idan ka koreni daga nan ban san inda zamu je ba ba mu da kowa” “Ba ku da kowa daga sama kuka fado? Daga ina kuka taso kuka dawo nan? Ku koma can ni bana son ganinku anan, ku bar min gida na fada muku idan na sake zuwa na tarar da ku a nan sai na wulakanta ku” Yana fadar hakan ya bude motarsa ya shiga, sauran mutane da suke tare da shi suka shiga dayar motar suka bi bayansa. Kallon mahaifiya dake kuka nai ina kwalla sai kuma na daga kai na kalli yar bukkarmu, miye laifin mu dan mun raba a wannan gidan tunda ba a ciki muka zauna ba, miye laifin bukkarmu mu dan kawai mun zauna a ciki. “Yau ko mun shiga uku an koro mu can nan kuma an kore mu, yau ina za mu?” Shine abunda mahaifiyata take fada ya yaren buzanci tana kuka. Zuciyata ta sosu sosai tana da gaskiya domin idan har kuma bar nan ban san wani guri da zamu iya rabawa ba, domin ba mu san wani gurin da zamu iya zuwa mu nemi taimakon gurin zama ba. Daga ni har Nana haka muka wuni cikin damuwa da rashin walwala har garin Allah ya waye, da safe Nana ta aika Lukman ya siyo mana waina ni da shi ita kuma ta gagara cin komai. Sai dai hakan be hanata fita bara ba, ni ce dai ban je ba, daman yau bana jin fitar saboda abunda ya faru jiya na laka min sata da kuma zancen barin gurin da muka raba, sai duk haka yasa ni jin kamar ma bani da lafiya, sai dai yau na samu yin sallah biyu a cikin lokaci tun a gida na wuni kuma bana aikin komai,  wato azahar da la'asar ban da Asuba da da nai bayan rana ta gama bayyana. Can da yamma Nana ta dawo har da biredinta a hannu, Lukman na bayanta da gorar ruwansa rataye a wuyansa. Biredin kawai muka ci muka sha ruwa sannan ya dauko kudin da ta zo da su da sauran kudin da suke rage mana idan mun siye abinci gaba daya kudin ba su wuce dubu uku da yan kai ba. “Wadannan kudi ba zasu iya mu kama haya ba, ni ban san yadda za mu yi ba” Magana take ina karantar tashin hankalin dake zuciyarta har yake bayyana kansa a fuskarta, ni dai na yi shiru ina ta tunanin sama mana mafita. “Nana ko mu nemi gadi wani gida? Ta yadda zamu samu gurin zama” “Wa zai ba mace gadi? Idan mu mun samu ni ina zan iya tare barawo?” “Ai dan mu samu gurin zama ne” “Hakan ba zai yi ba, sai dai na bincika wani gurin ko Allah zai sa mu samu” Tun daga ranar kullum Nana cikin neman gurin da zamu koma mu raba take amman ba mu samu ba, yawancin inda muke samu duka filaye ne mu kuma muna tsoron zama a fili sai dai a kangon gidan da aka fara aka bari ko kuma ba a karasa ba ko ya kuma ginin daya soma zubewa.   A kullum da fargabar zuwan Alhajin muke kwana mu tashi muna ta zuba ido ko zai zo amman shiru be sake zuwa ba har aka kwashe kwana kusan goma shabiyar, hakan yasa muka koma muna rayuwarmu ta yau da gobe cikin kwanciyar hankali. Musamman ni da ban sake saka wannan bakin mutumen a idona na ba. Yau ma da gari muka karya duk kuwa da kasancewar bana sonsa amman babu yadda na iya dole na ci ko babu dadi, bayan mun gama sha ne na tashi nai alwalar isha'i na kabbatar sallah. Ina cikin sallah na ji ihun Nana waccw ta kewa a bandaki kasa karasa sallar nai jin ihun yayi yawa na dauki fitilar hannu dake dakin na fito waje da sauri ni da Lukman muka nufi kewan ina Haskawa sai na hango katon maciji ya nade gurin daya yana ta zuro mana kansa, Nana kuma ta fadi gefe daya tana ta murje murje da alama cizonta yai ko kuma sara, Lukman ya saka kara ni kuma na saki fitilar a firgice na ruga izuwa titi cikin hudun hangon gidan ina neman masu taimaka mana, daman na san ba za a rasa irin wadannan abubuwan ba a guri kamar wannan, musamman da dare ba hudu yake zageyemu har sai idan mun kunna kara ko fita ko kuma hasken farin wata, wutar nepa kan sai dai mu hangota a manyan gidaje. Da ihu da karaji na isa titin gawon nama ina ta neman wadanda zasu taimaka mana, mazan da suke zama a gurin titi suka yo kaina da sauri ni kuma na shiga gaba ina gudu suna gudu har muka dawo cikin kangon gidan dake cike da hudu, masu wayoyi suka kunna wayarsu suka haske bandakin sai Nana aka gani babu macijin babu labarinsa, motsin kirki ma bata iya yi da sauri wani yace a bashi kyale sai ya daure inda yake zaton macijin ya tsareta wato kafar data rike. “Ku nemo Napep? A kaita asibiti” Daya daga cikinsu ya fada ni da Lukam babu abunda muke sai kuka ni ina rike da ita Lukman kuma yana tsaye bayana, a gurin wasu samarin ke kallo domin yau babu wannan bakin gentleman n a fuskata mai hana kowa ganin ainahin kyawo na. Ban san wanda ya kira Napep din ba nadai ga an shigo da ita har gurin Bukkarmu samarin suka rikata suka sakata ciki ni Lukman na shiga gaba ni kuma na zauna baya tare da ita ina hawaye kamar ba gobe. Ko wane motsi nata jinsa nake cikin kashina ji nake kamar ciwon a jikina yake, mahaifiyata ita ce duniyata, na gwada kokarina akan tsagaita kukana sai na gano ashe ni ba ba Jaruma ba ce a gafen dauri. Wata asibitin kudi mai zaman kanta Mai Napep din ya kaimu a lokacin da muka isa emergency sai suka karbe mu da gaggawa aka wuce da ita ciki Mai Napep ya juya yai tafiyarsa ni da Lukman sai muka yi tsaye waje. Har sai da Nurse din ta dawo kirana ta dauki sunan Nana ta bukaci naje wani guri na karbo kati sai na tuna da babu sisi a tare da ni, adole na bar Lukman a gurin na fita na hau achaba na je na dauko kudinta gaba daya na dawo naje na biya kudin katin sai kuma aka ce likita na son ganina. Da sauri na nufi inda Nurse din ta nuna na tura kofar office din na shiga hankalina a tashe fuskata duk hawaye ya bata ta, hannuna rike da yar jakar da Nana take zuwa da ita bara wacce kudin suke ciki. “Nurse tace kana son ganina” “Ke ce wa?” Likitan ya tambayata yana min wani kallo daga sama zuwa kasa, duk wanda ya kalli sutura baya bukatar na fada masa cewar ba mu da shi, tufafin da nake saye da su kawai sun isa su isarda sakon talaucin da muke tare da shi. “Mamata na kawo wacce maciji ya tsara” “ina Babanku?” “Babanmu ya rasu” “To ina yan'uwanku da ke zan yi Magana” “Ko minene likita ka Fada min mamata bata da kowa a nan sai ni, duka yan'uwan mu suna nijar” Na Fada idona na sake cika da kwalla. Kallo yai sai ya sake kallona sannan yace. “Okay wannan allurar za ki siyo naira dubu ashirin da daya za ki kashe” Ya Fada yana mika min wata farar takarda. Ina karba na juya jiki ba kwari zan fice sai na ji ya ce. “Kina da kudin ne? Idan ba ki kawo maganin nan da wasu hours ba Mamaki zata iya mutuwa” Juyowa nai idona na zubar da kwalla ma girgiza masa kai dan bana ko iya magana. “Babu?” Na gyada masa kai. “Bude baki kiyi magana wannan asibiti na ce zan iya taimaka miki idan baki da su” “Wallahi ba ni da su ban san inda zan samo ba, bara mu muke kamin mu saye abincin” Shiru yai kamar mai nazari, sannan ya kalleni ya ce. “Shikenan zan mata allurar kuma zan ya mata tiyata na cire dafin macijin” Da sauri na risina kasa ina masa godiya wani irin jindadi ya rufe jin za a ceci mahaifiyata sai dai ban taba jin inda akai wa wani tiyata aka cire dafin maciji ba sai dai allura. “Taso muje ki saka hannu a file” Da sauri na mike tsaye ina share hawayena, yana gaba ina binsa har muka shiga wani daki mai cike da nurse da yawa ya dauko wata takardar ya miko tare da nuna min inda zan saka hannu. Hannunsa ya dora saman nawa yana yimin sigh din yadda zan hi daidai, ina daho kaina nai arba da wata nurse tana girgiza min kai alamar kai, sai dai ban gane abunda take nufi ba na tausayi ne ko kuwa na kar nai yi ne oho ni dai fatana a ceto mahaifiyata.... https://my.w.tt/GuQH5GZKb9 *Z A K I* By Khadeeja Candy 4️⃣ Misalin goma aka shigo da ita tiyata amman basu fito ba sai karfe uku da wani abu na dare. Anyi mata tiyata cikin nasarar Allah da iyawarsa, saidai a halin da naga mahaifiyata sai na kara matso da maraicin mu kusa ni da Lukman. A wani dakin mai kyau aka ajeta kamar matar wani babban mutum ko kuma wata hajiya, a jikinta an manna mata wasu na'urori har a hancinta a wani abu mai kamar kwanfuwuta nake kallon tafiyar numfashinta, sai dai tana kwance a gurin kamar gawa jikinta babu tufafi sai wani zanen asibiti da aka saka a lulluba mata. Ina tare da ita har asuba ban runtsa ba, gani nake kamar zata iya farkowa ta bukuci wani abun ko da yake babu komai a tare da ni wanda zata iya ci ko ta sha, lukman ne kawai ke ta bachinsa hankalinsa kwance. Misalin takwas da rabi likitan ya shigo cikin shiga ta kananan kaya da rigar likitoci a samansu fuskarsa a sake yana ta min murmushi kamar mun saba. “Ina kwana?” Na gaisheshi cikin girmamawa. Sai ya amsa min kamar be gane ni ba, ba kuma kallon rashin ganewar bane, wata kila sai a yau ne yake tantance irin hallittar da Allah yai ta kyau mai daukar hankalin mace balle kuma namiji. “Miye sunanki?” “Aisha amman ana kirana Ataa” “A nan kuka kwana?” Ya tambaya yana kara tantance kyawun surar jikina. “Eh” “Ayyah ban sani ba ai da na kawo muku abun shimfida ko kina da shi” Na girgiza kai alamar aa a cikin yanayin dake nuna dukan hankalina da damuwata tana gurin mahaifiyata ne. “Da gaske baki da kowa a nan Nigeria? Ku yan nijar ba naga akwai wadanda suke da yan'uwa a nan ba?” “Ni ba mu da su, ba a mu da kowa a nan” Na fada masa cike da gundira da tambayoyinsa. Sai naga yayi murmushi kamar wanda jin hakan yai masa dadi, sai ya saka hannunsa aljihu ya nufi mahaifiyata yana dubata. “Ki samo riga ki saka mata da zanen da zai iya rufe kafafunta, na bada a siyo mata maganin dubu dari da bakwai manyan magunguna ne masu tsada yadda mahaifiyarki za tai saurin jin sauki kuma an mata allurar bayan na mata sai nai mata operation na cire mata dafin macijin” Wani irin dadi ne ya lullube ni sai na rasa ta inda zan fara masa godiya, hawayen farinciki suka cika ido har naji kamar na dauke shi na hade, a rayuwata ta duniya tunda Nana ta haife ni ban taba karo ko ganin mutum mai tausayi da jinkan masarasa irinmu ba kamar wannan likitan. “Na gode Allah ya biyaka ya saka mata da alheri, Allah ya daukaka asibitinku Ya saka maka da aljanna ka taimaki rayuwata sosai ba zan taba manta ka ba” Murmushi yai yasa hannunsa aljihu ya ciro kudin da za su kai dubu goma ya miko min. “Ga wannan, ki je ki siya abinci ki yi duk abunda kike bukata, kuma idan mahaifiyarki ta farka ki kirani karki bata komai” Wannan karon addu'ar gamawa da duniya nai masa, domin a tunani ita kan aljannah da duniyar duka ya sameta, domin mutum mai taimako mai share hawayen masara shi Allah yai masa alkawarin aljanna kamar yadda Annabi yace shi da mai taimakon maraya kafada da kafada za su shiga aljanna da shi. Babu abunda nake hangowa sai matarsa tabbas tayi dacen miji domin samun miji mai taimakawa al'umma har su yi masa addu'a ta yi babban dace. Bayan ya fice ne na kama hannun Lukman muka fita zuwa gida, sai dai abunda na tarar a gidan sai yafi tada hankalina fiye da ciwon mahaifiyata. Yar bukkarmu ce aka hankade can gefe aka cire kwannon da maihaifiyata ta saka domin zagaya yin fitsari ko ba haya, kayan abincinmu da tufafinmu an watsar da su can gefe gaba daya an watsar da komai. Tsaye nai ina kallon yadda kayan idona cike da kwalla, ba komai yasa ake mana haka ba sai rashin, rashi kuma na kudi saboda talaucin da yake tare da mu da kuma rashin kowa a kusa da mu. Lallai muhalli babban abu ne, da ace haya muke ko mallakinmu ne da wani be isa ya wulakanta haka ba saboda kawai mun raba a gidansa dan mu zauna. “Ataa waya maka mana?” Lukman ya tambaya yana bata fuska kamar zai yi kuka, ban da jansa jikina na rumgume babu abunda nai domin ina jin idan har na bude baki nai masa magana kuke kawai zai fito domin shine cike a zuciyata. Waiga nai banga kowa ba, da alama ba aikin yau ba ne idan kuma har yau akai shi tabbas tun da farar safiya aka zo aka mana haka aka tafi. Bani da wani zafi daya wuce na share hawayena na shiga hada tarkacen mu ni da Lukman babu inda zan kaisu gashi ni kuma ban iya hada bukkar ba balle na sake yin wata, Nana ce ta iya hadawa ita kuma tana asibiti, ance zuciyata tana ga mai kudi idan aka masa abu sau daya ba za akara ba, domin zai dauki mataki wanda bashi da shi kuwa sai ayi ta maimata masa kuma ya shanye yai hakuri saboda bashi da shi, ganin babu inda zan kai kayan yasa na hada komai na je can cikin wani daki da yake a kangon gidan da ba a karasa ba na saka su ni da Lukman sannan na fito waje na samo duwatsu na hada murhu na dauki jaran bukkarmu na saka na aiki Lukaman ya siyo mana ashana da taliya da cefanen dafa taliyar. Ni kuma na wanke tukunyar da mike girki da ita sannan na gyara tarugu da albasa na nufi gidansu kawata Farida dan na jajjaga, da nai sallama mahaifiyarta na ji taki ta amsa min a zatonta rokin wani abun na zo kasancewar wani lokacin idan ba mu da ashana ko gishiri tana aikawa tace ta sammata, har take yawan cewa wai mun cika roko, ni ko a ganina duk wanda zai mika maka hannu yace ka bashi tabbatas oa fishi kuma dan kana da shi ne ake zuwa nema a gareka amman mutane da yawa ba su fahimci hakan ba. Sai da na karasa har bakin kofarta ina sallamar sannan ta amsa min na gaisheta ta amsa ciki ciki. “Dan Allah turminku za ara min zan jajjaga tarugu ne” A tsaye ta bar ni a gurin na kusan minti biyar tana ta kallon arewa 24 a karamin tv ta sannan ta dago ta kalleni. “Gashi can gidan kin gama ki dauraye” Ta fada min a cikin yanayin da ke nuna alamar bata son ara min kamar yadda take yawan yi min idan na zo nema abu, shiyasa bana son zuwa idan ba Farida ce a gidan ba ita ce mai min maraba wani lokacin har ta tayani dakawa duk kuwa da irin fadan da mahaifiyarta take mata na kin jinin abotarmu da take. Ni kuma babu wani gida da zan iya zuwa na roki abu kamar irin gishiri ruwa ko ashana ko daka wani abu kamar wannan gidan, domin duka gidanjen da suke kewaye da mu na manyan mutane ne, a ina zan iya shiga roko ayi min kallo banza wani gidan ma ko gate din su ka taba sai mai gadin yace maka basa nan saboda kawai anga yanayinka na masu bukata ne. Daf da zan gama jajjagen ne take tambaya wai ance maciji ya tsari mahaifiyata, ni kuma na amsa mata na kuma bata labarin yadda abun ya faru har ma da taimakon da aka mana a asibiti, sannan na kwashe jajjagen na wanke mata turminta kamar yadda ta bukata na yi mata godiya na juyo na fito. Hura wutar na fara yi na dora tukunyar na zuba mai da sauran abubuwa a take saboda tsananin yunwar da nake ji, haka nai ta bankawa girkin wuta har ya dafu na zubawa Nana a wani kwanon mai murfi Lukman kuma na saka masa a nasa kwano na zubawa kaina, na kwashe saura a wani kwanon na rufe, sai na zauna na tisa abincin a gaba na kasa ci babu komai a zuciyata sai kewar mahaifiyata da tunanin ruguje mana bukka da akai, a take na nemi yunwar na rasa, kuka ya maye min gurbinta har sai da Lukman din ma ya fashe da kuka ganin yadda nake ta kuka. Abincin na aje na shiga ciki na daukowa Nana riga da zane na saka a jakar da kudin suke ciki na jira Lukman ya gama cin abinci ya wanke hannunsa sannan na dauki abincin Nana muka fito bakin titi na tari Napep muka shiga ni da shi muka doshi asibitin. ALIYU POV. Bachi Rahama take ta yi tun bayan sallah asuba har goma ta gota, a saman wani katon gado mai tsada da katifa mai kyau take kwance, ta lulluba da blanket mai laushi kamar kada, ta saba da hutu da jindadi haka take bachi har sai ta gaji dan kanta ta farka. A lokacin Aliyu na falo zaune saman wata lallausar kujera rike da kofin tea laptop a saman ciyoyinsa yana duba yanayin yadda aikin gas din kamfaninsu na Abuja yake tafiya. Sanye yake da short jean da farar vest, a gabansa wani katon tv ne mai dauki da farar baturiya tana watso labarai a channel din Al Jazeera. Wayar ce dake silent tai haske sai dai be lura ba, domin ya cire ringing din, baya so hayaniya ko kadan that's why he choose Abuja a gurin aikinsa to because its a quiet place for him, ko da wani meeting din ne ya taso wanda yasan za a iya hayaniya da cece kuce sai ya tura abokinsa Umar. Be lura da kiran ba har sai da ya gama abunda zai yi ya juya da zimmar aje laptop din sai ya hango wayarsa tana haske, hannu ya kai ya dauki wayar ganin Doc Asim yasa shi sauri picking. “Hello Doc” “Ranka ya dade ina ta kira baka dauka ba” “Yeah ina wani aikin ne, sai yanzu na lura” “Na kira na maka albishir ne cewar an samu Kidney din” Kofin tea dake hannunsa ya aje ya mike tsaye da sauri cike da farinciki marar misaltuwa har ya saka shi kin yarda da maganar da Doc ya fara masa sai da ya sake tambaya duk kuwa da yasan be taba masa karya ba. “Doc are you serious?” “Wallahi da gaske nake, gani nan ma gurin Alhaji abunda muke tattaunawa kenan” “Wow gani nan zuwa” Yai saurin waje wayar ya nufi bedroom dinsa cike da farinciki, labulayen dake fuskarta gadon ya bude sai ga hasken rana yana haske gadon kasancewar gaba daya gaban dakin glass ne. Jin hasken rana yasa ta lunkumewa cikin blanket tana bata fuska, sai ya zauna bakin gadon ya yaye blanket din ya dagota. “Dear wake up yau ranar farinciki ce” “Ba yau na ke birthday ba sai next month” Ta fada ba tare data bude idon ba. “Ba maganar birthday za ki yi birthday cikin koshin lafiya In-Sha-Allah, Doc Asim ya kirani ya fada min yana gurin Daddy suna tattaunawa an samu Kidney din” Ba idonta kadai ta bude ba har da baki da da hancinta duk a bude suke jin wannan daddan labarin, da sauri ta kama hannayensa. “Dear da gaske” Ya gyada mata kai yana kallonta da cat eyes dinshi sai ta rungume shi da sauri ta fashe da kukan dadi. Dan murmushi yai kadan ya shafa bayanta. “Congratulations Dear you save me” “I said i would” Ya fada yana dagota daga kirjinsa yana share mata hawayenta. “Tashi ki shirya zan kaiki gidanku ni kuma na wuce gurin Daddy na gana da likitan naji yadda za ayi” “I love you” Ta fada tana kuka, sannan ta daga daga jikinsa ta sauka ta shiga bathroom ta sauka cikin kankanen lokaci ta fito shima ya shiga yai ko daya fito har ta shirya, shima be dade gurin shiryawa ba dan ya matsu ya hadu da likitan. “Idan munje can zaki karya promise?” “Promise” Ta fada tana saka bakinta cikin nashi, musanyar yawu sukai halshenta da nashi suka hada auratayya sannan ta sake shi ya rika hannunta suka fito tare. A tare suka sauko kasa hawayen farinciki tana cika idonta, har ya bude mata motar ta shiga sannan ya zagaya ya shiga ya yai mata key tun kamin yai horn mai gadin ya bude masa gate suka kama hanya gidan Alhaji Nasiru Gobir. Cikin kankanen lokaci suka isa gidan nan ma horn daya yai aka bude masa gate, tun kamin yai parking Rahama ta bude motar ta fita ta shiga cikin gidansu da sauri, shi kan sai da ya faka motar sannan ya fito ya rufa mata baya. A falo ya sameta tana zaune kusa da mahaifinta. “Daddy naga kamar kana cikin bacin rai” “Wallahi wasu wulakantaccin mutane suka shige min a gidan da nake ginawa a Clapperto road, ance sun janyo har macizai suna shiga gidan, amman na ce a korasu” Hannunsa ta kama. “Daddy kar wannan ya dame ka yau rabar murna ce na Doc Asim ya kira wai an samu kidney din” “What” Gaba daya suka amsa har kanenenta suka taso ta sauri suka rumgume ta suna ta murna. Alhaji Nasiru ya kalli Aliyu irin kallon ganin kima da kauna ta suruki da surukinsa. “Mun gode sosai Aliyu Allah ya saka da alheri” “Karka damu Alhaji aikina samawa Mamata lafiya ko ta hali yaya, zanje gida san na samu ganawa da likitan” Daga haka yai musu sallama ya fito ya shiga motarsa ya dauki hanyar family dinsu wato gidan Alhaji Garba Fayau... _________________ Wayyo Ataa 😪 https://chat.whatsapp.com/DaDP34cM3s5FMfaQOtFM9Y *Z A K I* By Khadeeja Candy 5️⃣ Ko da mu ka isa asibitin ana ta mopping ko'ina, ni da Lukman muka rakube kamar sauran talakawa irinmu, wadanda suka tsaya suna jira a gama mopping din sannan mu wuce, masu hannu da shuni kan da masu galihu wucewa kawai suke ba tare da n tsayar da su ba, masu aikin sai mika musu gaisuwa suke. Mu kam mu kai tsaye har aka gama mopping din sannan na mika kafata na taka sai wata daga cikin Nurses din da suke tsaye a can babban kofar shiga ta daka min tsawa data saka hantar ciki ta kaďawa. “Ke ki ka fi kowa a nan ne da za ki tsallako ki wuce gurin be gama bushewa ba” Da sauri na koma baya na tsaya gurin da na ke tsaye dazu, sosai tsawar nurse din ta firgita, da alama idan na sake taka gurin zuwa za tai ta mareni. Ina rike da hannun Lukman da jakar dana sakawa Nana tufafin dana dauko mata, Lukman kuma na rike da taliyar da ke cikin kula mai murfi dabam kular ma dabam. A haka muka tsaya a gurin kamar wasu marayu har gurin ya gama bushewa, da na ga wasu sun fara takawa sannan muka taka muka doshi ciki, sai kuma muka tarar dan cikin ward din be gama bushewa ba wani gurin ma a yanzu ne ake mopping din.   Dan Albarkar likitan nan yana tsaye da wasu nurses suna masa wani abu a takardu, yana hangomu ya ce mai mopping din ta tsaya mu wuce, cikin sauri ta tsaya muka fara takawa zuwa inda dakunan suke, wani dadi na ji ya lullubeni ko ba komai ya nuna min karamci da kulawa a matsayina na ba kowa ba, a take na ji kimarsa da darajarsa ta karu a idona. Sai da na gaisheshi sannan na wuce dakin da Nana take ciki, nurse din nan ta jiya na tarar wacce ta ce rika girgiza min kai lokacin da zan saka hannu a takardun da aka yi wa Nana aiki. “Ina kwana?” Na gaisheta cikina cike da tsoro gani nake kamar ita tsawar zata daka min kamar waccan nurse din. Sai na ga ta amsa min da lalama tana min kallon tausayi. “Lafiya kalau, wannan matar mamarki ce” “Eh mamata ce” “Ina Babanki ya ke?” “Baba na rasu?” “To waya kawo ta asibiti?” “Ni na kawo ta” “Ba ku da kowa nan ne?” Na dan yi shiru ina nazarin irin tambayoyin da take min da suka yi kama da wadanda likitan can yai min dazu, ban san dalilin da ya saka suke son yi min irin wadannan tambayoyin ba. Har na bude ba ki na bata amsa sai ga likitan nan ya turo kofa ya shigo yana waya baki har kunne sai dariya yake, sai dai ganina da wannan nurse din yasa yai hanzari katse wayar ya hade fuska kamar be taba dariya ba. “Me kike a nan?” Sai nurse din ta sha jinin jikinta ko motsin kirki bata yi. “Na na na... Zo duba... Ta..” “Ke duba ta ke kika aje ta? How dare you? Fita ki ba ni guri” Kamar zata 6ace 6at a gurin haka tai saurin ficewa jikinta sai rawa yake kamar mazari, a nan nima na shafawa kaina lafiya fahimtar cewa yana da fada sosai na koma gafe ni da Lukman muna kallonsa. Yana kallona sai ya sake fuskarsa yai min murmushi yana kallon jakar hannuna. “Miye a ciki?” “Kudin da ka ba mu ne, da tufafin da ka ce a daukowa Nana” Na amsa cikin tsantsar ladabi da kuma muryar da ke nuna babu ruwana. “Wannan fa” Ya sakw tambaya yana kallon kular da ke hannun Lukman. “Taliyar da na dafa ce na kawo ma Nana ko za ta ci” Dariya yai yana kallon murfin kular da ke daban da kular wacce ta soma koredewa wani 6angare na jikinta ma har ya tsage. “Ya ma sunanki?” “Ataa” “Ataa karki sake kawo abinci a nan asibiti, zan sa a rika kawo muku na safe da na rana da kuma na dare ke da kanenki da kuma Mahaifiyarku idan ta farko kinji?” “Da gaske?” Na fada ina kara girmama kirmarsa lallai a cikin dubu samun mutum kamar wannan likitan mai tausayi da taimako sai an tona. “Yes” Har kasa na kai idona cike da hawaye ina masa godiya kamin na koma yi ma Allah godiya daya hada mu da irin wannan mutumen. Karasa yai ya duba Nana ya canja mata wasu abubuwan na na'ura sannan ya juyo ya kalleni. “Ina tufafin suke?” “Ga su” Na mika masa da sauri a zatona saka mata zai yi sai naga yai baya da sauri kamar mai kyama. “No no bari na kira wata ta saka mata” Daga haka ya juya ya fice, ni kuma na kuma kusa da ita na tsaya ina ta kallon fuskarta ga ta a kwance kamar ta mutu, amman fuskarta na kyalli kamar zata bude baki tai mana magana. “Ataa yaushe Nana zata tashi?” Lukman ya tambaye ni yana kallonta. “Ni ma ban sani ba” Na amsa masa idona taf da hawaye tausayin mahaifiyata ya cika zuciyata, na san Allah ne ya kaddaro mata haka amman macijin nan be kyauta min ba. Ina tsaye wata mata mai zubin marasa mutuncin ta turo kofar ta shigo fuskarta ta tsage tana sanye da uniform din nurse sai wani kallo take watsa mana a hankade. “Ke kamar ki za ki ace ba ki iya sakawa mahaifiyarki riga?” Ta fada tana fisgar rigar a hannuna sannan ya karasa gurin Nana, yadda ta saka hannu ta tallafota sai ta tsikar jikina ta tashi dan zaka rantse da Allah ka ce karamin yaro ta dauka, a gabana gaban Lukman ta janye mayafin da aka rufe Nana da shi ni da Lukman muka ganta tsirara haihuwar uwarta ga dinki a cikinta gurin yayi ja sosai kamar jini ya kwanta, da sauri ya juyar da fuskar Lukman ni ma na juya muka ba ta baya hawaye na sauko min, ban juyo ba sai da na tabbatar ta gama ta rufe mata zane har na watsa min wata magana marar dadi jin. “Tufafin ma duk ďoyi suke yi mtswwwww” Ni dai ban ce mata komai ba na karasa gaban Nana ina kallon yadda yake ya mutsa fuska duk da kasancewar bachi take ko kuma ma na kira shi da suma, da alama taji zafin yadda nurse din ta motsa ta, ji nai kamar ace ina da wata dama da zan bawa ciwon umarni ko kuma na saka hannu na dauke mata shi ta farka ta tashi mu bar asibitin nan, ga dukan alamu likitan nan ne kawai mai mutumci sauranka ko kallo ba mu ishe su ba. A kujerar da ke gaban gadon na zauna ni da Lukman sai ya kwanto jikina kamar wani maraye yana ta tabe baki alamar zai yi kuka, ni kan daman hawayen kawai na ke ina jin wani abu ya tsaya min a zuciyata.   Kamar yadda fada haka kuwa akai misalin uku saura na rana aka aiko mana da abinci irin na manyan restaurant mai dadi har da naman kaza, a take Lukman ya hau murna jikinsa har rawa yake ya dauki naman kazan ya kai baki, ni kan sai na ji bana son cin komai duk kuwa ni da irin kwadayina. A bandakin na shiga nai alwala nai shimfida dankwalina nai sallah azahar, babu komai a sujida ta sai rokon Allah ya bawa Nana lafiya.    ALIYU POV.   Yadda ya ke driving sai ka rantse da Allah ba jiransa ake ba, hankalinsa a kwance yake tukin motar yana tafiya kadan-kadan duk kuwa da irin son ganin Doc Asim da yake. A ka'ida ba ya danna horn sau biyu sau daya ya ke yi amman wannan karon sai da ya danna har sau uku sannan mai gadin ya bude masa gate, tsayawa yai dai-dai gurin mai gadin ya sauke gilashin motarsa yana watsa masa wani kallo na marasa ganin talaka da daraja ya ce. “Kar ka yarda na sake danna horn har uku ba ka bude min gate ba” “Ayi hakuri ranka ya dade, Wallahi na dan zagaya ne” Dattijon mai gadin ya fada jikinsa na rawa. “An aje ka nan ne dan ka zagaya?” “Ina nufin bandaki na shiga” “Kai ya shafa ni dai na fada maka next time korarka za'ayi” “In-Sha-Allah hakan ba zai sake faruwa ba, ayi hakuri Zaki” Uffan be sake ce masa ba ya faka motarsa a harabar gidan sannan ya fito yana ta kanshin turaren da ke sanar da zuwansa ya shiga falon. Khaleesat da Hauwa na zaune a falon ko wace rike da waya, ganinsa yasa sukai mugun shan jinin jikinsu suka natsu sosai ko kallon inda yake ba sa yi gudun kar ya su hada ido da shi ya ce sun masa ba dai-dai sun san shi sarai ya tsani kallo. Ganin Momy da Daddynsa yasa ya saki fuska ya cire talkamin kafarsa ya karasa kusa da su da sallama. Dukansu fuskarsu dauke take da murmushi da alama suna cikin jindadi da farinciki. “Dan wajen Fulani ka yi lattin zuwa likitan kuma ya ce yana da aiki da yawa a asibiti be tsaya jiranka ba ya tafi” Momy ta fada tana kiransa da sunansa da ta saba kiransa. “Ya ce min an samu kidney din” Ya fada yana mikawa Daddy hannu su gaisa. Sai Daddy ya dora da “An samu, na masa magana ya ce zai hada ku da wani likita da za ku je London ayi mata dashen” “Samun Kidney ba abu ne mai sauki a yanzu ba, gaskiya likitan nan ya cancanci komai daga gurina, at long last Rahma zata samu lafiya” “Ba daga gurinka ya cancanci komai daga garemu ma gaba daya, amman ina fatar ba ta wani ya cire ba, domin ba kowa zai yarda ya bada kodarsa ba” Aliyu yai shiru kamar mai nazari can kuma ya kalli Mommy ya ce. “Ba lallai ya zama haka ba, kin san Nigeria ce, akwai talakawan da ba su san darajar kansu ba, za su iya siyarwa saboda kudi” “Amman ko talaka sai wanda talaucinsa ya kai makura gaskiya, ai sai da lafiyar ake neman kudi” Momy ta fada with doubt. Aliyu yai murmushin kasaita. “Momy kenan ba ki san talaka ba, na san Doc Asim zai iya siye zuciyar talaka da kudi ya samu abunda ya ke so, domin ya san shi ma zai fanshi fiye da haka a garemu, shi fa talaka wawan mutum ne, indai za ka nuna masa kudi to zai maka komai na duniyar nan” “Wato ďan wajen Fulani kai da Maman ka Fulani ban san wanda ya fi wani kyamar talaka ba, su ma fa mutane kamar mu duka daya muke a gurin Allah” Ya kalli Momy cike da mamakin yadda take hakikancewa idan ana maganar talaka. “Momy kenan, ai Mama Fulani gaskiya ta ke fada, tsakanin mu da talaka sai dai akwai mu amfana da shi shi ma kuma ya amfana da mu ta hanyar biyansa hakkinsa, amman ni ko abota bana fatar ta hada ni da talaka” Daddy yai murmushi yana dafa kafardar Aliyu ya mike tsaye. “Sai ka yi hanzarin samun Doc Asim ku tattauna, kasan matsalar matarka ita dayar kodar na daf da daina aiki” “Yeah haka za ayi, san same shi mu tattauna, Thank you Dad” “Your Welcome” Daddy ya fada yana nufar hanyar da zata sadashi da part dinsa. Momy kuma ta mike tsaye tana fadin. “Talaka ba shi da kima a idonka kai da uwarka Fulani” “To ai ba shi da kimar ne Momy ki ce kin ki gane sai hada shi kike da mu, bayan kuma ba daya ba ne, as long as ba da ganganci Doc Asim ya cire kidney din nan ba babu abunda zai dame ni, ni zalince ne kawai ba na so, indai na san na biya ka to dole ka min aiki ba wani uzuri da zan dauka, so indai siyenta Doc Asim yai ni ya kyauta min wlh kuma zan bashi fiye da abunda zai tambaya” Ya fada yana mikewa tsaye ya nufi dinning area, wani kebantaccen guri ne da ya kusan ayi babban falo da shi amman ba a zuba komai a gurin ba sai kato dinning table da freezer, daya daga cikin kujerun dinning din yadi aja ya zauna yana kallon Momy wacce ta taso ta nufo shi tana fadin. “Ba ka ci abinci ba ka fito? Matar ta ka har yau ba ta iya girkawa ta baka ba?” “Momy kin san lafiya be isheta ba, kodar ďaya da ke jikinta ma ance ta fara lalacewa, so ba komai na ke bari tai ba, and Momy kin san wahala ai sai talaka” “Au ni da nake shiryawa Daddynku fa?” Murmushi yai kadan yana dora duka hannayensa saman dinning din. “Ai ke Momy saboda kin kwana biyu ne, ke da kina da kurciya ai Daddy ba zai bari ki yi girki ba, i rather na yi oder a restaurant da nai forcing dinta ta girka min, besides ba komai ta iya girkawa ba ita a gidansu ba aiki take ba” Momy ta tabe baki tana saka masa sikari kwaya biyu a kofin tea. Bayan ya gama karyawa ya sauko daga dan stairs din dinning din yana taba wayarsa ya nufi kofar fita kanensa na mika masa gaisuwa. Kai kawai ya daga musu ba tare da ya amsa musu ba sai kara hade fuska yake kar su ga damarsa. Fitowa yai harabar gidan yana amsa kiran Rahma, da yai picking shiru yai har sai da ta fara magana cikin yanayin damuwa duk da irin faduwar da gabansa yai jin muryarta kamar tana cikin damuwa. “Dear ina driving na kade wani” “Hope babu abunda ya faru?” “Ya ji mu a kafa da kai” “Lafiyarki na ke tambaya” Ya tambaya kamar maganar bata son fitowa daga bakinsa, sai dai tashin hankalin da ke zuciyarsa da burin jin lafiyar matarsa ya saka shi fidda numfashi kadan-kadan. “I'm fine amman shi mutumen ya ji ciwo” “As long as be mutu ba, ba wata damuwa ba ce, turo min address din inda kike yanzu” Be jira abunda zata ce ba yai hanging, he don't mind ya tambayi inda zata je ko abunda ta je yi, saboda ya yarda da matarsa ko kasar zata bari bata fada masa ba ba damuwarsa ba ce indai zata je kalau ta dawo kalau. In few minutes ta turo masa sakon inda take sai ya forward massage din to the one of his bodyguard. _Ka samu Madam a wannan address din, ka biya wanda ta kade ko dubu nawa ya ke so, and make sure matata ta isa gida lafiya_ Yana tura masa sakon ya mayarda wayarsa aljihu ya nufi motarsa yana wani shan kamshi. ATAA POV. Hankalina ya tashi sosai lokacin da na ga yamma ta gabato mahaifiyata bata ko matsa ba balle ta bude ido, ban san kan aikin asibiti ba, amman a yadda na ke jin ana cewa ko tiyata akai wa mutum indai ya kwana ya wuni yana farkowa sai dai tawa uwar shiru. Ina ji ina gani yunwa ta saka ni a gaba tana ta cina ni kuma na gagara kai ko da ruwa a bakina na natsu ina ta sauraren kukan da cikina ya ke min. Shiru shiru babu wanda ya sake leko dakin likitan be dawo ba, sai da yasa an aiko mana da abinci dare, a nan Lukman kawai ya ci ni kasa ko da kallon abincin balle na kai hannu na ci.    Bayan na gama sallah isha'i ina ta kaiwa Allah kukana, sai na hango Nana na motsa har tana yawo da kanta, da sauri na mike na tsaye na rika gadonta ina kiranta cike da jindadi. “Nana Nana Nana” Shiru bata amsa min ba sai juya kan take yana dantsar baki kamar bata cikim hayyacinta, ban yi dabarar na je kiran nurse ba balle kuma likita sai kawai na daga zanen da aka rufa mata na ga inda aka mata dinki yana fitar da jini kadan-kadan  ganin hakan yasa na fita daga dakin da sauri na nufi wani dan guri mai kamar reception inda nurses da yawa maza da mata suke tsaye wasu kuma a zauna. “Mama ta ta motsa amman bata magana kuma na ga jini gurin da aka mata aiki” Na fada cike da damuwa, sai duk suka tsaya suna min wani kallo kamar na kyama, a nan na kalli tufafin jikina hakika na yi dauda sosai tufafin da ke jikina wadanda na saba sakawa ne kullum, kuma ba damuwa nai da na wanke ba, gashi dazu na ji girki da kara sun kara datti, sai dai ba da dauda na ke a yanzu ba ta lafiyar Nana na ke. Daya daga cikinsu taja tsaki kamin ta aje biron da ke hannunta ta nufo ni tana fadin. “Ni Wallahi ba son irin kazaman patient din nan na ke ba, idan kuma ba ka kula su ba ace ba ka yi aikin ka ba” Sai sauran suka saka dariya, sai duk na ji na muzanta na ji babu dadi amman hakan be hana ni binta a baya ba ita kuma tana gaba har muka shiga dakin. https://chat.whatsapp.com/HlKVwXU1HwlIrs8jJeHHqZ *Z A K I* By Khadeeja Candy 6️⃣ ALIYU POV. Kamar kullum idan zai kwanta sai ya tsaya ya duba wasu abubuwan a laptop dinsa haka ma idan ya tashi da safe musamman abubuwan kamfaninsu na samar da gas wato Sky Global Resources, babban kamfani ne da babu irinsa a nigeria wanda ke samar da gas da man fetur da ma hako wasu ma'adanai na kasa da saffara su, kuma shi yake wakiltar babban reshensu da ke Abuja inda ake tura komai, hakan yasa dole komai rashin lokacinsa dole ya matse a haka ya kula da wasu abubuwan. A dakinsa ya ke amman ko'ina n dakin kanshin expensive perfume din Rahma yake, yana daf da rufe laptop din Rahma ta turo kofar dakinsa ta shigo hannunta rike da mug, bakinta ya sha janbaki har kyali yake, wata rigar bachi ce a jikinta mai kamar rariya, komai na jikinta a bayyane yake kamar ma bata saka ba komai ba. Dagowa yai yana kallon yadda ta nufo shi tana wani irin taku kamar kwararriyar karuwa, da fuskarka ta miskilanci, a lokacin da ta karaso kusa da shi sai ta kurba ginger tea dake cikin mug din a bakinta ta saka dayan hannunta ta dauke laptop din dake jikinsa ta aje gefen gadon da yake zaune ta raba kafafunta biyu ta hau saman cinyoyinsa ta juye masa tea a bakin. Murmushi yai bayan ya hade tea ta karbi mug din hannunta ya aje kan bedside drawer ya wutsilo da ita saman gadon ya zama na shi ne a samanta yana ta kallon bakinta wanda ya sha janbaki. “Kin san lafiyar jikinki bata ishe ki ba, amman sai neman fitina, idan kuma na biye miki ciwon ki ta shi ko?” Ya fada mata kadan kadan kamar mai rada yana ta yawo da cat eyes dinsa a fuskarta. Murmushi tai ta san halin Ali Zaki baya wasa da wannan bangaren komai fushin da yake ko damuwar da yake ciki, duk miskilancinsa da jin kansa indai ta wannan bangaren nan na da nan za'ayi saurin kama shi. “Ina ta tunanin abunda zan yi na saka maka ne, Aliyu kana kokarin kawarda duk wani abu da zai taba ni, a sadakar a lokacin da likitan nan ya fada min cewar kidney ta daya ta samu matsala, bayan kuma an cire daya, na dauka mutuwa zan yi amman gashi yanzu za amin dashen wata na samu lafiya” “Komai zan miki Dear, na yi magana da Doc Asim dazu da rana har ya hada ni da likitan da za muje UK tare da shi, In-Sha-Allah within week din nan za mu gama duk wani shirye-shiyen sai muje can a saka miki, i will pay Doc Asim a huge of money saboda wannan abun da yai min, zan yi masa godiyar saving a billionaire naira wife” Ya fada yana kissing din wuyanta, tare da saka halshensa yana wasa da gurin. “I promise you idan kika samu lafiya ba zan raga miki ba” Ya fada sound so sexy kamin ya shiga aika mata da sakwanni masu zafi....... ATAA POV. Lokacin da nurse din ta shigo ta dubata sai ta kalle a hartsine ta ce. “Farkawa ne za tai, kuma wannan jinin ai dole ya fito tunda jiya akai tiyatar be gama bushewa ba” Nurse din ta fada kamin ta kalleni. “Ga ki kyakkyawa kin maida kanki kazama” Ko kadan ban kula wata maganarta ba, wani dadi na ji ya lullube ni jin cewar farkawa ne Nana za ta yi, sai raina ya fara fari, wani irin shauki ya kamani na ji kamar na taba ta tai magana, ina ta kallon Nana kamin na maida dubana gurin Nurse din yadda ta saka tufafinta da yadda take aikinta sai ya burgeni daman na dade ina ganin sha'awar aikin likita ko unguwar zoma amman ba ni da wannan halin hali saboda ba ni da wannan gatan na karatu, wa na ke da shi da zai tsaya min nai karatu har na kai ga zama nurses ko likita? Ni da karatun secondary ma ya gagareni sai bara da aikin titi.   Bayan ta fice na zauna a kujerar dake facing dinta Lukman kuma yai kwance kasa yana jin bachi, ido na kura mata tun ina kallonta da kyau har bachi ya soma sata na, shigowar likitan ce tasa na Nana tana bude idonta tana rufewa kamar bata san inda take ba. Ni nai saurin mikewa tsaye likitan kuma yai saurin karasowa kusa da ita ya shiga dubata sai na ga yana ta murmushi. “Masha-Allah tiyata ta yi kyau, na sunanta?” “Nana” Na bashi amsa ina wani irin murmushi da ke bayyana irin farincikin da ke raina. Sai ya shiga kiran sunanta cikin ikon Allah da iyawarsa ta amsa muryarta can kasa kasa. “Na'am” “Sannu” Ya ce da ita a lokacin da ta kalleshi. Sannan ni ma na fada. “Sannu Nana” Sai ta kalleni ta gyada min kai sai kuma ya dan dago kan kadan ta kalli cikinta da ke lullube da zane. “Ina Lukman” “Gashi yana bachi” Na bata amsa da sauri. “Waya kawo ni asibiti?” “Ni na kawo ki maciji ne ya tsare ki, shine wannan likitan ya taimaka ya miki tiyata ya cire miki dafin kuma yai miki allura ya siya miki magani” “Allah ya saka da alheri” Ta fada daker tana kallonsa. Sai ya cire mata wasu abubuwan da ke jikinta ya kalli Lukman. “Bari a samo muku abunda za ku rika kwana ko, ba ki san ana dauka cuta kasa ba da za ki bar shi ya kwanta” Na yi shiru bance komai ba, shi kuma ya juya ya fice daga dakin. Be jima ba ya dawo tare da wasu masu sharar asibitin su hudu ko wannensu dauke da abubuwan bukata, tabarma ce da babban bargo da filo da kuma buta da carpet din sallah, dayan kuma abinci ne ya kawo mana. Wallahi sai na rasa da wanne baki zan yi ma likitan nan godiya da irin dawainiyar da yake da mu ko da shi ya haifi Nana iyaka kenan yadda yake kashe mana kudi sai ka ce ya sanmu. “Za a kawo muku kayan tea gobe, ai kin iya gada shayi ko? Sai ki rika hada mata tana sha da fruits” Ya fada bayan mutanen masu shara sun fita. “Dan Allah ya sunanka?” Na tambaya cike da fargabar yadda zai amsa min. “Ina son na rika saka ka a addu'a ta ne idan nai, irin alherin da kake mana yayi yawa kana ta dawainiya da mu kamar ka san inda muka fito” Kallo yai n wasu yan mintuna kamin ya dauke kansa tare da wani guntun numfashi ya ce. “Ba komai ba sai kin min addu'a ba, Allah zai ba ni lada ai” Yana fadar hakan ya juya ya fice, ni kuma na bishi da kallon kauna kauna irin ta wanda ya taimake ka a halin da kake da bukatar taimakon. A dare Nana ta dan ta6a fira da ni tana tambayar abubuwan da ke mana ina ta fada mata ita kanta tai farinciki sosai kuma tai masa addu'a sannan ta sha kankana kadan kamar yadda ya umarta, ni ko a daren sai da nai tas na ci na koshi sannan na kwanta kan shimfidar da ya kawo mana ni da Lukman, kusan sai na ce ban taba kwanciya akan wani abu mai dadi makamancin katifa ba irin yau. Tun daga lokacin kullum Nana cikin kara samun lafiya take, ni da Lukman kuma ba mu kara zuwa bara ba, kudin daya bani tun a karon farko ma ban sake taba su ba domin komai na ke bukata yi mana yake babu abunda muke yi da kanmu tun kama daga abinci magani da duk wani abun bukata. Sai dai abu daya yake ta bani tsoro, yadda Nana ta gagara komawa daidai, motsi kadan sai ta rike kirjinsa ko gefen cikinta ta ce ciwo yake mata kuma tana yawan fadawa likitan amman sai ya ce ba wata matsala ba ce zata ji sauki nan gaba kadan. Mutanen da muka zaman arziki da su suna ta zuwa suna duba Nana, kusan sai na yi sati ban leka gida ba idan ma wanka zan yi sai na yi a bandakin da ke dakin, daman can kuma wanka ba damu na yai ba, iya kar kokarin da na ke a yanzu na tsayar da sallah a kan lokacij ne ganin bana aikin komai a nan asibitin sai zama, Nana ma ina kokarin ganin na saka ta yi duk kuwa da irin kin son taba ruwa da take ko da na zafi ne yanzu sai ta ji jikinta ya kara rashin karfi, ganin hakan yasa na samo mata kasa na koya mata taimama kamar yadda aka koyar da mu makarantar islamiya lokacin da na ke zuwa. Kullum cikin yi ma likitan nan da ban san sunansa addu'a muke ni da Nana, yana kulawa da mu sosai, ba dan rashin lafiyar Nana da ke cikin raina ba da Allah kadai yasan kibar da zan yi akan abubuwan dadin da muke ci, sai dai Nana kan ta kasa komawa yadda take a da, walwalarta kuzarinta da kuka sakewa ta kasa yi kusan kullum sai rama take daman can ba wani jikin ne da ita sosai ba. Wasa wasa muka kwashe wata daya a asibitin, har zaman ya fara gundirata ita kanta Nana da ke ciwon sai ta fara gajiya, kullum addu'ar Allah ya bata lafiya mu bar asibitin, kowa mamaki yadda dafin macijin ya zame mata haka ake yi, ko da yake likitan ya fada mana cewar dafin ya warke ciwon cikin cikinta ne kawai ya rage ya warke. kusan sai na saba da nurses din da ke dan shigowa duba wani lokacin amman masu sake fuska a cikin, sauran kan sai dai su yi min kallon banza, da kuma mutanen da ke zam waje harabar asibitin suna jinyar wasu, domin idan na gaji da zama cikin dakin da take sai na dauko tabarmar nai shimfida a waje ni da Lukman mu zauna, har ita wani lokacin Nurse Shukura tana fitowa da ita ta sha iska, duk a cikin Nurse din Shukuwa ta fi sake min sai dai a yadda na lura kamar shi likitan baya son shirinmu da ita, wata kila akwai rashin jituwa a tsakaninsu ne ko kuma wani abun oho, domin na lura da ita ma kamar bata jindadin yadda muke yabonsa muke saka masa albarka da addu'ar alheri. Haka nan kawai wani lokacin idan bata aikin komai sai ta shigo dakinmu mu yi ta fara kamar mun saba, ta haka har na san unguwar da take zama wato tudun wada da kuma inda ni ma nake zama har take ce min tana da wata kawa a kusa da mu, akwai ranar da take fada min cewar tana tausayina ni da Lukman jin cewar ba mu da kowa a nan Nigeria ko ma muna da su ni ban sansu ba, domin Mahaifina be tana fada min ba Nana ma bata nuna fada min ba, har take ce min ya kamata na nemi yan'uwa ko'in suke saboda wata rana. A lokacin na samu Nana na tisata a gaba ina tambayar wasu daga cikin yan'uwanta har take fada min harma da na Babana ma. Misalin karfe biyu da yan mintuna na fito daga dakin na nufo gurin da muke zama a harabar asibitin inda shuke-shuke na zauna. Ban yi minti hudu da zama gurin ba sai ga kawata Farida ta zo, na jidadin zuwanta domin yau harabar babu mutanen da muka saba fira wasu an sallame su wasu kuma suna ciki gurin kula da masara lafiya, wadannn bakin fuskar kuma sun tsare ni da idonsu, dukuwa da nasa wannan kallon baya rasa nasaba da irin kyauna da kuma manyan idanuwan da Allah yai min haka zalika gashin kaina, shiyasa ba kasafai na ke son yin alwala a waje ba sai gaka hankali kowa ya dawo kaina duk da kasancewar gashin nawa a cinkushe yake guri daya har wani warin tsami yake, domin ba kitso nake masa ba idan am anyi kitson sai warware saboda sulbin gashi, kuma ba damuwa nai da na wanke ba balle har na shace shi ko na gyara. Dambun da suka na masara ne ta riko mana, duk da kasancewar bana jin yunwa amman hakan be hana ni ci ba domin ina son dambu kusan duk wani abu da za a sarrafa shi da masara ko shimkafa ko dawa ina sonsa. Na ci dambu da yawa saboda yajin da aka cika a ciki domin ni ma'abociyar cin ya ji ce sosai, bayan mun gama fira ta shiga ciki ta duba Nana tai mata ta jiki sannan ta fito na rakota har bakin titin ringin sambo ina ta jin kamar na bita dan har ga Allah zaman asibitin ya fara ci min rai. A hanyata ta dawowa ne na hadu da Nurse Shukura tana sanye da uniform dinta amman ta dora bakar abaya sama ta rataya jakarta da alama ta tashi daga aikin ne zata tafi gida. “Anty Shukura kin tashi ne” “Eh sai kuma gobe, na kika fito?” “Wallahi kawata na raka ina jin kamar na bita, zaman asibitin nan na ishemu” Na fada ina yar dariya kadan, sai tai murmushi ta ce. “Zama kan ai yanzu kuka fara tunda har kika ga Doc Asim ne yake kula da ku, in ma kina son mahaifiyarku ta samu lafiya to ki dauke ta daga asibitin nan ki kaita wata ko ku koma a gida, idan ba haka ba Wallahi za ki iya rasa mahaifiyarki asibitin nan ballantana yana ganin ba ku da kowa kin ga asirinsa rufe ba wanda zai san dalilin mutuwar mahaifiyarku” Hankali na tashi da ji kalamanta har ya kasa boyuwa a fuska ta. “Me kike Nufi Anty Shukura?” “Bana nufin komai kawai baki ganin ciwon mahaifiyarki na ki ci ya ki cinyewa kullum kuna nan, ai ya kamata ki yi tunanin canja mata asibiti, kuma karki ce ni na baki shawara idan kin tashi kawai ki ce ke kin gaji gida za ku koma, Wallahi da masu kudi ne ku ko masu yan'uwan da yanzu an yi tunanin wata hanyar daban amman ba zama haka nan ba har kuna kokarin shiga wata na biyu asibitin nan, akan saran maciji kawai haba Ataa ke ma ai ya kamata ki yi tunani” Tana gama fadar hakan ta yi wucewarta ta bar ni nan tsaye ina ta nazarin maganganunta, gaskiya ta fada wani gurin tabbas da masu kudi fa yanzu an canja nata asibiti amman kuma mu ba kamar su ba ne, kuma idan muka ce za mu canja asibiti kudin magani dawainiya wa zai yi da mu? Na san dai ba za mu hadu da dan albarka likita kamar wannan ba. In ta wannan sake saken na nufi cikin ward din tare da tunanin wata kila likitan be kware sosai ba shiyasa ka Nana ta gagara warkewa garau. #Team Ataa #Team Rahma #Team Aliyu Masu yi ma Rahama addu'ar mutuwa ita ma lafiyarta kawai take nema ita da mijinta 😀 amman kun fara dora mata tsana tun ba a je ko'ina ba 😑 https://my.w.tt/PWohUhlPv9. *Z A K I* By Khadeeja Candy 7️⃣ Tunanin inda zan kai Nana idan na dauketa daga asibitin ya hana ni runtsawa a daren, ba ni da halin da zan iya nema mata magani a wata asibitin domin na lura maganin nata mai tsada ne kamar yadda Doc Asim yake yawan fada min cewar ya siyo maganin, a yadda yake hidima da mu idan na ce zan canja asibitin zai iya zargin wani abu ko ya ji babu dadi taya ma zan iya fada masa cewar asibiti za mu canja ai sai ya zargi ko mun raina Hidimar da yake damu ne? Da wannan tunanin na kwana na tashi na sake kwana na sake tashi a haka har akai kwana uku ban fadawa kowa ba, sai dai ta wani 6angaren Anty Shukura tana da gaskiya ya kamata na gwada aikin wani likitan ko Allah zai sa a dace ta koma kamar da, maganarta ta cewa indai ba son nake Nana ta mutu ba na canja mata asibiti na daga min hankali sosai har na saka samun sukuni, idan na shiga bandakin da zimmar alwala ko fitsari sai na zauna a ciki nai ta kuka, ban san abunda Allah ya tsara ba, ban san abunda zai faru gaba ba, Nana zata tashi ko ciwon zai yi ajalinta duka ban sani ba, zan rayu da ita na wani lokaci ko a'a duka ban sani ba. Iyakar abunda na sani kuma na ke da tabbaci akansa shine mutuwa kuma Allah baya barin wani dan wani, sai dai na san ina son rayuwar Nana fiye da ta kowa duniya, na rasa mahaifiya yan shekaru kadan a baya, sai na ji kamar ba zan iya hakurin na rasa Nana a yanzu ba. Bayan na yi kukan na wanke fuskata na fito na zauna a kujerar da ke fuskarta Nana, ita kuma tana daga zaune ta rame sosai sai sauke ajiyar zuciya take tana kallon mutane da ke kai kawo a waje ta window dakin, wani irin tausayinta ne ya kamani da kuma tausayin kaina a lokaci daya mace mai kuzari kamar Nana wacce zata fita bara tun safe ba zata dawo ba sai yamma ta koma a zaune tsayin ma wahala yake mata, lallai Allah kadai ya iya haka. “Nana” Na kira sunanta a hankali, a lokacin da ta juyo ta kalleni sai na ga hawaye a idonta, ba ta damu da sharewa ba saboda tasan na ga hawayen babu abunda zata boye min. “Wani gurin ne yake miki ciwo?” Na tambaya hankalina a tashe ina komawa saman gadon asibitin inda take zaune na zauna kusa da ita. “Tunani na ke yi, yanzu idan na mutu ke da Lukman ku za ku shiga wani hali, ba ku da gurin kwana ba ku da komai ban bar muku gadon komai ba sai na bara, ba ku da kowa a garin nan, a can nijar kuma babu wanda ya san inda kuke a nan balle su nemi ku, ba ku da gata yanzu sai na Allah Ataa, jo yanzu da wannan bawan Allah be taimaka mana ba da yanzu kila ka mutu” Iyakar kokarin da nai shine na rike kuka da hana hawaye taruwa a idona saboda ta karta gani jikinta ya kara yin sanyi. “Za ki ji sauki Nana In-Sha-Allah za mu koma can gida nijar tare da ke da Lukman mu yi komai tare” Na fada ina nuna mata kamar ban damu da hawayenta ba. “Wannan Nurse din Shukura ta bani shawarar wai na dauke ni daga wannan asibitin na kai ni wata” “A nan ma ai ana kula da kai, kuma kana samum kulawa da abincin duk ana baka da yaranka amman can idan ka je wa se baka?” “Ni ma na yi tunanin haka Kuma ina jim kunyar likitan ma, kar ya ce ba mu gode ba, amman ta bani shawarar na ce masa gida za mu koma” “Ataa kana karami kana ta wahala haka nan kullum, idan ka kai ka wani asibitin ina kudi?” “Akwai kudin da ya ba ni ya ce na siya abincin ranar ba na fada miki ba? Kuma akwai wada muka dan samu da aka zo ganin ki zai kai dari takwas idan mum hada dubu goma kenan har da yan canji ma, sai mu je wani asibitin mu gani ko za mu dace” “To ai sai ka fada mata ko?” Ta fada a nufinta na fadawa likitan. “Eh zan fada mishi amman ba za mu ce masa wata asibitin za mu ce masa gida za mu koma kin ji?” Ta gyada kai, kamar likitan ya san abunda muke tsarawa sai ga shi ya shigo dakin rike da wasu takardun fuskarsa a sake kamar kullum. “Ya jikin?” “Ka ji sauki” Nana ta amsa masa, sai ya ciro daya daga cikin takardun ya miko min. “An sallame ku, ya kamata ku koma gida hakan nan, ki cigaba da bata magani da zan ba ki kinji?” Na saka hannu biyu na kar6a cike ladabi da kuma murna. “Ai za ki iya ganewa idan an rubuta mikia jikin maganin ko? Kin yi boko?” “Eh amman bakin primary kawai ina karanta abu idan ba mai wahala ba ne, ko kuma idan hausa ce” Sai yai murmushi. “Ai na san ba kya ganewa kan” Yana rufe bakinsa wasu nurses biyu suka shigo dakin dayar tana rike da ledar magani dayar kuma tana turo wheelchair. A nan ya karbi maganin ya rika nuna min yadda za rika bata su kuma Nurses din suka dauki Nana suka saka ta a wheelchair din, sannan ya saka suka kwashe mana duka kayanmu suka fitar waje, ban ma san an samu napep ba sai da na nade tabarmu da ke waje na yi ma mutanen sallama na janyo hannun Lukman muka biyo bayan nurses din. “Allah ya saka da alheri ya biyaka” Ita ce addu'ar da muke ta masa ni da Nana, har aka saka ta Napep din ni ma na shiga Lukman na shiga gaba tare da mai Napep din. Sosai na so muje wata asibitin amman Nana ta ki ganin kamar za mu kashe kudi ne kawai, wai a ga magani nan ya ba mu kudin sai mu siya abinci da su a cewar ta, daman can Nana ba son kashe kudi take ba sai dole, balle wannan da take ganinsa da yawa har dubu goma. Har kofar kangon gidan mai Napep din ya kawo mu, sai na umarce shi daya shiga ciki ba musu ya shiga ciki, ni na fara fitowa na rika Nana ta fito tana tafiya ďuke dan bata iya mikewa tsaye dai-dai, Mai Napep din ya cire mana duka kayanmu da suke bayan Napep din ya aje mana zan ba shi kudi ya ce Doc Asim ya bashi sai kawai nai masa godiya na shiga da Nana cikin kangon gidan na samu wani guri da anke zaton sitting room za ayi da shi na shimfida mata bargon na kwantar da ita. Lukman ya shigo da sauran kayan, ni kuma na dauki tsitsiya na hau sharar gurin dan yai datti sosai, sai da gama share duk fadin gurin sannan na dawo kusa da ita na zauna. Wani dadi na ji a lokacin da na kalleta lallai uwa mai dadi idan bata a cikin gidan sai yai babu dadi, idan kuma tana nan sai naji dadi duk kuwa da kasancewar ba a lafiye take ba amman ina son ganin abata. Ba mu dade da zaman ba akai kiran sallah la'asar sai na tashi nai alwala nai sallah sannan ita kuma na debo mata kasa tai taimama tai sallah, ba a maganar Lukman daman shi tun da ya gama saka mana kayan ciki ya fita yawonsa. Sama sama muke ta firar mu da ita, yawancin firar da muke ta kwantar da tai asibiti ne mutanen da suka zo ganinta da kuma alherin da likitan yai mana, bayan sallah magariba na dauko maganin na sake bata kamar yadda ya fada min, da isha'i muka kwanta a gurin zuciyata cike da tsoro ina ta ganin kamar macijin nan zuwa zai yi ya sake tsaran Nana ko ni ko Lukman, amman Allah ya tsare mu har gari ya waye babu abunda ya same mu, yau ma ban yi sallah da wuri ba sai da rana ta fito, bayan na gama sallah na je na samu gawayi na wanke bakina sannan na ba Lukman kudi na ce ya siyo mana koko a inda ake saidawa da kosai da suga, ba laifi ta ci sosai ni ma na ci duk da kasancewar ina sha'awar waina amman bana son na siya bayan shan kokon gudun kar kudin mu su yi saurin karewa, kara kawai na hakura har zuwa gobe sai na siya da safe mu karya da ita gaba daya. Muna ciki zaune sai ga Farida ta zo, ashe jiya bayan dawowarmu daga asibitin ta je aka ce mata an sallame mu. Mun sha fira sosai ba tabar gidan ba sai da ta soma jin iskan hadari na tasowa alamar hadarin daya hade sama yana daf da tasowa. Sannan tai mana sallama ta tafi, tafiyarta da mintuna kamar hudu zuwa biyar na hango wasu mutane sun doso inda muke dukansu maza. Gabana ya dan fadi kamar yadda na Nana ma nasan sai ya fadi, suna isowa suka fara fisge dan zanen a muka saka muka tare kofar da shi saboda sanyi suka jefar. “Wai ku wasu irin mutanen? Ko wacan lokacin ba an muku magana ba, wato shine kuka dawo ko? Mai gidan yace mu koreku dan an fada masa kun dawo ashe ma cikin gidan kuka shige kuka zauna dan rainin hankali” “Dan Allah ku yi hakuri Wallahi mamana bata da lafiya kuma babu inda zata laba sai nan” Na fada ina kallon fuskokinsu na marasa imani da ganinsu irin yan sara sukan nan ne ya turo mana marasa tarbiya. (Area boys) Aiko kamar jiran suke nai magana sai biyu daga cikinsu suka dauki Nana suka kai ta can kusa da gate suka aje dayan kuma ya turani waje da karfi, Lukman da tsoro tuni na nufi inda Nana take da sauri idonta cike da tsoro, sai kuma suka shiga ciki suka fara shuri da kayan mu da ke ciki sai da suka fitar da komai da kafa sannan suka fito suka nufo inda na ke tsaye ni da Nana muna muka suka ce mana idan muka sake shiga ciki duk suka dawo sai sun sassara mu, kuma mu nemi wani wajen tun kan dare yai mana mu bar gurin kwanon da aka saka dan fara zagayewa kamar za ayi gate. A gurin muka tsaya ni da Nana da Lukman har aka fara ruwa, daga ni har Nana babu abunda muke sai hawaye Lukman na tsaye yana ta kallon ta bata fuska sosai kamar ya fasa kuka. Sai da naji an fara yayyafi sannan na rika Nana da zimmar mu koma ciki sai ta rike hannuna ta girgiza min ka alamar ba zata koma ba. “Idan an gama ruwa sai mu fito” Na fada da muryata ta kuka, sai ta girgiza min kai alamar ba zata ba, hakan yasa na nufi kayanmu na dauko bargon da likitan ya siya dan mu rika kwantawa ni da Lukman akai na lulluba mata na shiga ciki Lukman ma shigo muka fake a ciki ruwa na dukan kanmu. Wani abun Allah kuma sai akai ruwan da kama da bakin kwaya ga sanyi sosai domin har da kankanra suke. A take Nana ta fara tari jikinta na ta karkarwa jin hakan yasa nai saurin bude bargon sai na ga jini duk ya bata mata baki har ya sauko saman rigarta ashe tarin da take jini take fitarwa, rumgume ta nai na fashe da kuka ina daga kaina ina kallon ruwan saman da ke saukowa kamar a cikinsu wani zai kawo mana dauki.... Wayyo Nana 😪 https://my.w.tt/PWohUhlPv9. *Z A K I* By Khadeeja Candy 8️⃣ Sai da ruwan suka dan tsagaita sannan na samu damar mikewa tsaye ina daga Nana daga jikina. Ta galabaita sosai har wani lumshe ido take tana budewa amman wani abun mamaki idan ta kalleni sai tai min murmushi, wata kila so take ta kwantar min da hankali ganin irin yadda na ke ta kuka kamar ba gobe, a saman bargon na kwantar da ita duk kuwa da irin sanyin ruwa sama da ke jikinshi na nufi inda kayanmu suke na dauki Hijab dina da shima ya gama jikewa na saka a haka na fita daga kangon gidan da gudu zuwa nemam nepep, bakin titin gawon nama na fito duk wacce na tara bata tsayawa wata kila saboda ruwan be gama daukewa ba gashi dare ne, daker na samu wata wacce babu kowa a ciki ta tsaya da sauri na shiga ciki ina fadin. “Mu bi ta nan marar lafiya za mu dauko” Kamar yasan halin da nake ciki sai ya shiga kwanar Clapperto road da gudu muna kawowa kangon gidan na ce ya shigo ciki, da taimakon mai napep din muka saka ta ciki sannan na nufi jakar da kudin suke ciki na bude na daukosu gaba daya sun jike har sun hade guri daya, ni da Lukman muka shiga da sauri mai Napep din ya ja zuwa Uduth wato Usmanu dan fodio teaching Hospital, kamar yasan daman can nake son kaita. Ta sabon gate din emergency ya shiga da mu, ba laifi nurse din sun karbo mu hannu biyu sannan suka ce na je na karbo kati, da gudu na bazama cikin asibitin neman inda ake siyar da katin domin ban sani ba, hasali ma ban taba zuwa asibitin sai dai na bi na wuce, wata mace ce ta nuna min gurin da na isa ban samu layi sosai sai yan kwarorin mutane wata kila saboda yana dare ne. Amman a haka sai na kasa bin dan karamin layin na shiga rokonsu ina ta kuka. “Dan Allah ku taimaka min na karbi kati mamana zata mutu dan Allah” “Zo nan a baki” Wanda ke layin gaba ya fada sauran kuwa kallona kawai suke jikina shakaf da ruwa har diga suke a kasa. Gabansa na shiga na mika dari biyar a bani katin sai ya ce min basa son kudinbda suke jike, mutumen nan ya ciro dubu daya sabuwa hul ya miki na karba hannu biyu na ba mai bayar da katin sannan na rubuta sunanta ya miko min katin da chanjina kusan dari hudu ya cire har da yan kai, a wautata sai na mikawa mutumen canjin. “No rike, Allah bata lafiya” “Amin na gode” Na juyo da sauri zuwa inda mahaifiyata take, ina isowa likitan ya hau min tambayar ciwonta nai mishi bayani. “Maciji ne ya tsare ta wata biyu da yan kwanuka da suka wuce, shi ne na kaita asibiti likitan yai mata tiyata ya cire dafin macijin, amman yace ta daina taba ruwa bata son sanyi shine yau ruwan sama ya doketa ta fara tarin jini” “Dafin maciji ake yiwa tiyata? Allura dai ko?” “Aa tiyata yana nan a cikinta ma” Na fada ina girgiza masa kai. A take ya rubuta mana wasu abubuwan ya dauko wata takarda ya miko min. “Ku dauke ta yanzu kuje a mata hoto” Sai nurses din suka dora min ita akan wheelchair na soma turara muka fito daga dakin ina rike da takardar, daman Lukman na tsaye bakin kofar be shiga ciki ba. Da tambaya na isa gurin da aks hoto sai suka ce sai naje can wani guri na biya kudin sannan na kawo musu shaidar biyan, haka na barta a gurin na isa inda suka kwantanta min na bashi takardar da wacan mai hoton ya bani sai ya fada min kudin da zan biya. “Dubu biyu da dari bakwai” Na ciro kudin na bashi shi ma sai ya ki karba wadanda suka jiken wai basa son irinsu. “Innalillahi wa'inna ilaihirraji'u” Shine abunda na fada na ji kamar na dora hannuna a kai na kurma ihu iya karfina. “Kawo kudin haka” Ya fada yana mikon min hannunsa wata kila yaji tausayi na ne, a haka na mika masa dubu uku ya bani canji tare da shaidar biyan kudin sannan na juyo da guduna na dawo na kawo ma mai dauka hoton, sai da akai ma mutun hudu sannan aka shiga da ita aka dorata akan wani gado suka shafa mata wani mai a jiki suka dora mata wani abu mai kamar dutsin guga suna ta yawo da shi a cikinta. Bayan sun gama suka dora a kan kujerar wheelchair suka ce na fara zuwa na kaita can gurin likitan sai na dawo na karbi hoton. Haka na turata na koma da ita a dakin da ke cike da majiyanta na tsaya a inda likitan ya saka aka sauketa dazun na kira wasu nurses suka zo suka taimaka na dorata saman gadon, sannan na kama hanyar komawa, abun ka da mai hankali tashe sai hanyar ta bace min ita kaure mutane ba tare da na kula ba. Har na kai ga yin kaura da wani likita zan wuce na ji an fisgoni an dawo da ni. “Ke ba ki ga ni ne hala?” Sai na kalleshi amman bana iya ganin fuskarsa saboda hawaye na cika min ido. “Hoto zan karbo kuma gurin ya bace min” Na fada cikin kuka mai karfi. “Wow cute girl” Ya fada kadan-kadan sannan ya nuna min gurin. “Doc Muhseen yi sauri pls” Wani mutumen mai sanye da uniform din nurse ya fada sai mutumen ya sake ni da sauri yai gaba ni kuma na nufi inda ya nuna min. Ko da na koma har an fitar da hoton sai kawai na karbo ma juyo na dawo inda nurse din suke na mika musu sai suka nuna min dakin likita. “Can za ki shiga ki kai” Na doshi dakin da sauri na tura na shiga ina sallama can ciki saboda kuka. “Ga hoton” Na mika masa sai ya karba yana ta turanci da wani mutumen dake zaune a daya daga cikin visitors chairs, likita yai rubutu cikin wata farar takarda ya miko min. “Idan ki siyo ka bawa nurse su saka mata” Na karba da sauri sannan na fice duk abunda nake Lukman na biye da ni a baya a duk inda na saka kafata dana dauke sai ya saka tasa. A nan ma sai da na tambaya aka nuna min pharmacy sannan na kai takadar su ma suka ce sai na je wani guri kusa da inda ake bata kati na biya kudin maganin da suka rubuta min a jikin takardar, haka na juyo cike da jin haushi irin tsarin na nu na wahalar da mai rai na je na mika takardar sai ya fada min cewar zan ba shi dubu biyar da dari uku da naira arba'in, a nan ma sai da nai ta roko sannan ya karbi jikakkun kudin ya bani yan canjina sai na koma can na kaiwa mai pharmacy ya bani amfanin da ledar sakawa. Kamar yadda likita ya fada min haka na mikawa nurses din sai suka hau dora mata ruwan suna saka maganin a ciki sukai nata allurai sannan suka dora ragowar maganin akan wani dan karamin abu mai kamar bedside drawer, sai ta sauke wani irin ajiyar zuciya bachi yai gaba da ita. Ni kuma na koma dakin likitan Lukman na biye da ni a baya na tura na shiga, har yanzu magana yake ta yi da mutuman dazun. “Na ba su sun saka mata” Sai ya dago ya kalleni yana dago hoton ya ce. “Ba dafin maciji ke damun matar nan ba, gurin da aka cire mata koda ne ke mata zafi maybe ayi aikin yadda ya kamata ba” Ji nai kamar ban ji abunda ya fada daidai ba, har sai da na sake tambaya cike da tantamar. “Ban gane ba koda kuma?” “Yes an yi mata tiyatar koda ko?” “Aa ba ayi ba” “Gashi nan hoto na nuna matar nan bata da koda ďaya, kuma gurin da aka cire kodar ne ke mata ciwo” “Ba a mata tiyatar ko da ba likita, maciji ne kawai ya tsareta aka cire dafin” “Ba ama cizon maciji tiyata allura kawai ake, wannan tiyatar koda ce aka cire mata” Ji nai kamar ba a duniyar nan na ke ba, sama na ke kasa na ke sai na kasa tantancewa yawu suka cika min baki daman can ido suna ta aikinsu na hawaye. Kar dai ace likitan nn ya da taimake mu kodarta ya cire? Kar dai duk taimakon da yai mana na siyen kodarta ne? “Amman dan kara tabbatarwa ki je ki yi wannan babban hoton” Ya miko min wata takardar. Da na cira kafar na je na karbo sai na ji kamar an rike ni kafafuwan suka lauye gurin daya suka min majiyar kamar wacce ta shekara a tsaye. “Wane likita ne yai mata tiyatar yace za a cire dafin maciji?” “Wa... Ni... ” Na amsawa likitan maganar na fito min a rarrabe. “Ya cuce ku ne kawai ko kuma an gada kai da shi an cuce ku, amman dafin maciji ai ba a masa tiyata” Daker na karasa na karbi takadar ya juyo kamar kazar da kwai ya fashewa na fito daga dakin likitan ina hawayen da ban ta ina ake turo min su ba. Ban san nawa hoton zai ci ba amman tun da ya ce babban hoto nasan sai ya ci fiye da dubu da wani abu da wacan karamin hoton ya ci, gashi sauran kudin da ke hannuna ba su kai ma dubu uku ba. Da wowa nai kusa da ita na zauna a kujerar roba da ke gabanta, ta bude baki tana sheda da nan da alama numfashin da ke fita daga hancinta baya isarta. Wani irin tausayinta ne ya lullube ni ina ta kallon fuskarta kamar yau na fara ganinta, taya zan iya fadawa Nana ya cire mata koda? Taya ma zata rayu ba koda? A tunani idan mutum ya rasa wani abu daga sassan jikinsa mutuwa zai yi. “Shikenan Nana shikenan” Na fada ina jan Lukman na rumgume, sai na saka kaina cikin jikakkar rigarsa na fashe da kuka marar sauti, ganin haka ba yasa shi ma ya fashe da kuka yana ta kallonta. ALIYU POV. Babbar asibiti ce kuma kwararriyar a duk fadin duniya, tun da aka ce za a mata dashen a can a cire dayar wacce ta fara lalacewa sai ya hankalinsa ya kwanta domin manyan likitocin ne za su mata aiki kuma sun san kan aikinsu. Within week din da suka je London aka yi mata aikin cikin iyawar Allah da ikonsa aka yi nasarar cire wacan kodar aka dasa mata wata. A can aka cigaba da kula da ita har na tsawon wata daya a ciki wata na biyu ne suka sallamota ta dawo gida Nigeria tare da mijinta da kuma mahaifiyarta wacce sukai tafiyar tare. A nan gidan ma kusan kullum sai Doc Asim da wani likitan Doc Jonah sun zo dubata, sosai ta so su tare a Abuja tun dawowarsu daman a can suke zama, amman Aliyu ya ki saboda yana son ya koma Abuja da zama a halin da matarsa take bukatar lokacinsa, ya san duk yadda ya ke son bata kulawa idan har suka je Abuja dole ne sai ya leka office amma a nan yana tare da ita tun safe har dare. At early morning ya farka yau kamar yadda ya sabawa kansa tun da suka dawo gida. Da kansa ya shiga kitchen ya saffara mata abunda zata ci idan ta farka sannan ya dawo falo ya zauna yana duba wasu abubuwan a laptop dinsa. “Aliyu...” Ta kwala masa kira daga dakin da take kwance duk da tasan ba zai amsa ba amman ta san zai ji ta, daman can baya amsa kira idan aka kira sunansa, sai dai idan yana kusa da kai ya kalleka ko kuma ya taso ya zo idan shine a kasa da kai, idan kuma kai ne a kasa da shi sai dai ka je ka same shi. Laptop din ya aje ya mike tsaye ya nufi upstairs fuskarsa ba yabo ba fallasa. Zaune ya sameta saman gadon ta dukunkune da bargo ta wani bata fuska kamar karamar yarinya. “Sanyi na ke ji waya ce ka kunna ac” Sai ya kai hannu ya kashe ac ya hauro saman gadon ya yaye blanket din da ta lulluba da shi yai kissing fuskarta. “Ta so muje ki karya kin san sun ce ki rika karyawa ba sai kin ji yunwa ba” “Me ka dafa min” “Doya da madara ka san kina so ai” “Ba ka iya ba fa” “I try ” Ya fada, yadda yake amsa maganar sai na rantse da Allah ba a bakinsa take fitowa ba, domin babu wata alama da ke nuna cewar magana yake. Saukowa yai da ita saman gadon ya nufi bandaki da ita da kansa ya wanke mata baki as usual sannan ya fito tare da ita. “Gidan nan duk yai datti kuma bathroom din ma yai wata ba a wanke ba ni kyamar Shiga ma na ke” Ta fada masa a daidai saitin kunnensa ba ce da ita komai ba ya ja suka nufi hanyar fita daga bedroom din. “Ka ji?” Nan ma be ce komai ba har suka sauko downstairs, daman can haka yake kamar wanda maganar take masa wahala, kujera yaja mata ta zauna akan dinning. “Ba ka ce komai ba” “Za mu samu wanda zai rika mana shara da gyara gida” Ya fada sannan ya zauna ya shiga serving dinta, da kansa yake feeding dinta har ta koshi sannan ya zuba ma kansa ya ci. “Yaushe za ka samo?” Haka ta dinga tambayarsa amman be ce mata komai ba, har ya gama cin abincin ya tashi. “Ni wannan miskilancin na ka damuna ya ke” A dai-dai lokacin da zai stairs ta fadi haka, sai kawai ya juyo ya sakar mata murmushi gefen fuska ya juya ya haye sama. ________ An ciye kidney din wata an raya wata 😪 https://my.w.tt/PWohUhlPv9. *Z A K I* By Khadeeja Candy 9️⃣ A saman kujera na kwana a zaune ina ta kallon Nana tun ina kuka da hawaye har na koma ina ta rare kukan kawai babu hawaye. A kasan gurin Lukman ya kwana. Tun da asubar fari masu sharar asibiti suka tashe Lukman ni kuma suka ce na fita za su gyara gurin. Ba dan babu yadda xan yi ba da ba zan fita ba, domin ina jin kamar idan nai nisa da Nana mutuwa za tai ta barni. A haka na fito ward din ina jin zuciyata babu dadi, Lukman kuma na ta murja ido alamar bachin be isheshi, kai tsaye gida na nufa kai tsaye domin samawa Nana abunda zata ci da ita da Lukman, wannan karon da kafa na iso kasancewar daga unguwar Clapperto zuwa uduth babu wani tazara sosai ga talaka irina wanda ya saba da tafiyar kasa. Ina janye da hannun Lukman har muka iso kangon gidan. Tsaye nai ina ta tunani ta inda zan fara, rashin lafiyar Nana ta tsaya min a rai har na so min kamar bana da wani sauran kuzari. “Ataa ya me za mu yi?” Maganar Lukman ce tasa na dawo daga dogon tunanin da nake rakiyar zuciyata da shi. “Koko zan siya maka kai da Nana” “Ni ba zan sha ba” Ya fada yana mitsintsika ido. “Saboda me? Ko waina kake so?” “Aa bana son komai Nana na ke son ta samu lafiya, Ataa ai zata tashi ko? Zata ji sauki ko? Na yi mafarki ta samu sauki tana min magana” Wani irin tausayinsa da na kaina nd ya lullube ni a lokaci daya, duk yadda na ke shakuwa da Nana nasan Lukman ya fini shakuwa da ita domin shi karamin yaro ne, kuma kusan kullum tare suke zuwa bara tsabanin ni da wani lokacin na ke zuwa wani gurin dabam. “Zata ji sauki idan kana cin abinci,Nana tana son ta ganka kana cin abinci” “Haka ta fada miki? Da na yi kwana ta farka?” Na gyada masa ina hawaye, sannan na saki hannunsa na shiga neman tsohuwar butarmu kuma basasshiya cikin duhun asuba, na yi alwala na mikawa Lukman ragowar ruwan shi ma yai alwala, wani masallaci na bi na gabatar da sallah magariba bata, na yi ma Nana addu'ar neman lafiya, sai kuma na rasa wacce za yi ma Doc Asim, bana son nayi masa mummunar addu'a ya zama ba gaskiya ba ne, domin har yanzu zuciyata tana min kwankwanton cewar ba gaskiya ba ne idan ma ya cire wane amfani zai yi da ita wane amfani zata masa? Mi ma zai yi da ita? Wata kila kuma siyarwa zai gi idan ana siya, waya sani ko wani ya ce ya cire? Amman kuma wa Nana ta sani da har zai sa ayimata haka? Ko shiyasa aka Anty Shukura ta ce mu bar asibitin idan ina son mahaifiyata araye? Shiyasa ta rika girgiza min kai a lokacin da zan saka hannu a takardar nan? Gaskiya ne idan har ba cire mata koda yai ba, mi zai sa yai ta taimakonku haka da yawa magani ma kadai ya kashe mata kudi mai yawa, abinci ma shi yake siya mana, anya idan ba wani abun zai mana taimako haka mai yawa? Haka dai zuciyata tai ta min wasiwasin gaskiya da kuma akasinta a lokaci daya. Fitowa nai na tsinci kwanon mu a inda mugayen mutanen suka harba mana kayan cin abinci da kafa na wanke na bawa Lukman yaje ya karbo mana koko, bayan ya dawo na sake aikensa ya siyo ma Nana waina mai yaji dan nasan ita ce favorite dinta. Kadan na kur6a kokon shi ma dan ina jin kamar bana da kuzari ne wai ko zan dan samu karin karfi, na mikawa Lukman sauran kokon ya shanye ba ko suga. Sauran ragowar kudin na fito da su ina kargawa da na hada sai na ga ba su kai ma dubu uku ba gaba daya dubu biyu ne da dari hudu da naira talatin, haka na hada kudin guri daya, na kurawa Lukman ido ina ta kallonsa yana shan koko duk da kasancewar hankalina a gurinsa ya ke ba. Bayan ya gama na dauki wainar da ragowar canjin mu doshi asibitin ni da shi ina tafiya ina jin kamar ana turani gabana sai faduwa yake. Lokacin da muka isa asibitin sai masu gadin ward din suka hana mu shiga, wai ba a zuwa ganin marar lafiya sai da yamma haka dokar asibitin ta ke. “Ba ganinta na zo ba, abinci na kawo mata kuma ni nake jinyar ta” Na fada cikin muryarta ta gajiyayyu mutane marasa galihu. “To bari likitoci su fito sai ki shiga” Na koma gefe na tsaya kamar yadda na tararda wasu mutanen a tsaye, ina nan zaman jiran likitonci su fito wata Nurse ta fito daga dakin tana tambayar mai jinyar Asma'u Ummaru. “Ga ni nan” Na fada da dan kuzarina. “Shigo ciki ana nemanki” Na bi bayanta kamar yadda ta umarta Lukman kuma ya biyo sai securiting ya rike shi a nan ya fasa masa ihu kamar zai tashi kunnuwansa a dole ya sake shi ya biyo bayana. Kusan likito ci hudu ne tsaye akanta ta farka har sun tashe ta ya dan jingina da gadon tana kallonsu bakinta ya bushe sosai har fatar bakinta ta fara kankara kamar wace ta shekara ba ta sha ruwa ba. “Ke kike jinyarta?” Daya daga cikin likitocin ya tmabaya yana kallona, wata kila gani yake kamar na yi karama ko kuma kyauwo na yake kallo oho. “Eh ni ce wani abun ne?” “Babu wani babba sai ke?” “Bata da kowa sai ni, ni ma kuma ba ni da kowa sai ita” “Ina hoton da na rubuta miki jiya kin yi?” Sai da yai maganar na iya gane daya daga cikin likitocin wanda ya karbe mu ne jiya da muka zo. “Ban yi ba, sai yau zan je na yi” “To kije ki yi, yana da kyau a kara tabbatarwa, abu na biyu kuma karki kuskura bata komai ta ci drip din da aka saka mata ba zai bari ta ji yunwa ba, ba za ta ci komai ba sai an yi mata hoton an kara tabbatarwa” “To na gode” Na fada cike da sanyin murya, sannan dayan ya miko min wata farar takarda. “A siyo mata wadannan magungunnan” “To” Na fada bayan na karba, sannan na zauna a kujera ina hawaye, su kuma suka nufi wata marar lafiyar dake kusa da mu suna dubata. “Sannu Nana” Na fada ina jin kuka kamar zai kubuce min, sai tai murmushin karfin hali ta ce. “Yauwa, Lukman” Ta mika masa hannu sai yaje da sauri kusa da gadon ya tsaya yana share hawayen kukan da be gama ba har yanzu na rokewar da wacan securiting yai masa abun ka da mai tsoron mai uniform. “Mi akai maki? Kin ci abinci” “Na sha koko, wacan dan sandan ne ya rike ni wa ba zan shigo ba” Ya fada yana hawan gadon ya zauna, sai ta kalleni. “Ke kin ci abincin” Kai kawai na iya gyada mata alamar na ci din, sannan na mike tsaye. “Ina zaki je Ataa?” Ta tambaya da yaren buzanci, ni kuma na bata amsa da hausa. “Zuwa zan yi na tambaya kudin hoton da maganin na ji ko nawa ne” “Kar ma kije tun da kin san ba kudi da mu ba” “Ba ki sani ba ko kudin ba shi da yawa, kara dai na tambaya na ji, idan da yawa sosai sai mu hakura” “To Allah yasa ba bu yawa, akwai ragowar kudi da yawa a hannu hannunki?” “Eh akwai” Duk wannan maganar da yaren buzanci mu kai sannan na mike tsaye na fita jiki babu kwari, sai da na tsaya bakin kofar na fadawa security cewar zan dawo kuma ni ce ta dazun mai jinyar marar lafiya gudun kar ya sake hana ni shiga idan na dawo. Wannan karon ban tambayi kowa ba na nufin gurin hoton sai suka rubuta min kudin hoton a jikin takardar dubu takwas da dari biyu wai babban hoto ba ne wanda za a ga duka sassan jikinta a jikin hoton. Sannan na doshi pharmacy na mika musu takardar suka duba suka rubuta min kudin maganin shi ma dubu biyar da yan kai, dukan ya tashi kusan dubu goma sha dubu ba dari uku, ji nai kamar na dora hannuna saman kai na kurma ihu, sai dai idan nai ihun wa zai taimake ni wa zai tausaya min har ya kawo min a gaji, a halin da na ke a yanzu ni kaina tsoron taimakon na ke duk wanda zai yi kare ni da zimmar taimako matukar ba ni na nema ba, na yana da wahala na iya amincewa da shi. Tafiya na ke kaina a kasa idona na zubar da ruwan hawaye, jin na ke kamar fuskata za ta taba kasa saboda maso min da tile din da nake takawa ake ina ganinsa kusa da ni. Kallon da na ga mutane na min ne yasa na share hawayen na daga kaina sama har na iso ward din na shiga, yadda na bar Nana haka na sameta Lukman na kusa da ita tana ta mata firar mafarkin da yai. “Kudin na da yawa ko?” Ta fada tun kan ji ta ji domin yanayin fuskata ya nuna hakan. “Su na da yawa amman za mu iya samu idan muka yi bara, sai na hada da wandanda suke hannuna” “Ataa kudin da za muke samu a bara ba su da wani yawan da za mu iya siyen magani” “Zan yi kokarin na samo su cikin sati biyu, ni da Lukman za mu yi In-Sha-Allah za mu samu kuma za ki samu lafiya Nana” “Ko dai mu koma asibitin wacan likitan?” “Aa ba sai mun koma ba, ba kuma za mu koma ba har a bada” Na fada cike da zafin rai. “Amman ya taimaka mana ai” “Eh ya taimaka mana ya ceto ranki daga saran da maciji yai miki, sai dai yanzu tiyatar da yai miki duk ita ce ta ja mana wannan matsalar” “Cewa sukai wani abu ya samu tiyatar ne?” “Aa cewa sukao maganin da kika sha ba shi ya kamata koli sha ba wai likitan be kware sosai ba” A take naga hankalinta ya tashi, har fuskarta ta kara boyewa, nasan da na fada mata gaskiyar cewar kodarta aka cire wata kila zan iya rasata ma a nan take. Matsawa nai kusa da ita ina kokarin kwantar mata da hankali. “Nana ki kwantar da hankalinki zan samu kudi zan biya a baki magani, kuma za ki warke za ki tashi, domin sun ce idan aka ba ki maganin za ki iya jin sauki a take” Hawayen idonta ta share tana sauke ajiyar zuciya tare da saka dayan hannunta ta dafe gefen hakarkarinta. “Nawa ne kudin maganin?” “Dubu takwas ne kuma akwai ragowar dubu biyar a hannuna, kin ga dubu uku kawai za mu samo” Na mata karya saboda hankalinta ya kwanta. sai ta lumshe ido hawaye suka sauko mata, ashe zubar hawayen mahaifiya yana da zafi da daraja a idon 'ya'yanta, domin a take na ji duk wani kuka nawa da na ke kokarin tarewa ya tafi sai na nemi rashin kuzarin na rasa, wani karfi da shaukin neman mafitar inda zan tsayarda da zubar hawayenta ya cika ni. Mikewa nai tsaye na juya da zimmar tafiya sai na ji Lukman ya kira ni. “Ataa zan biki ni ma zan yi baran” Hannuna mika masa ya mikon nasa na rika muka tafi daga ward din zuciyata cike da karsashi. Babban titin Gawon Nama muka fara yin baran, ganin ďan abun da muka samu ba mai yawa ba, yasa na ja hannunsa muka nufi titin gadar Alu ganin can din kamar ya fi manyan motoci, misalin karfe daya muka isa gurin bani da agogon da zai tabbatar min da hakan, sai dai ganin yadda rana ta soma budewa tana yin zafi yasa na fahimci hakan, gashi kuma wasu masallatan har sun fara kiran sallah karfe daya. Muna tafiya Lukman na ta bata fuska da alama ya gaji da tafiyar da muke a kafa, daga ni har shi sai gumi muke na wahala. Muna isa na nufi gurin wasu motocin shi kuma ya doshi wasu yana mika musu hannu, ba zan iya fadar abunda ya faru ba, iyakar abunda na sani an saki traffic motocin sun fara wucewa sai kuma na jiyo ihun Lukman da dukan karfinsa sai kuma na ji kaurar karafuna. Juyo nai a firgice ina kallon mutane da ke nufar gurin da sauri, wani irin kara nai da muryar da ban taba sanin ina da irinta ba, na saki kudin da ke hannuna na n ruga a guje ina haniniya kamar wani doki... ALIYU POV. Yana zaune sitting rooms dinsa yana duba wasu takardu da Nasir ya kawo masa tun daga Abuja domin ya saka hannu. “A nan ma kai za ka wakilce ni Nasir, ba zan iya barin Matata a nan na tafi saboda aikina ba” “Amman miyasa ba zaka dauke ga kuje can gaba daya, ai zaka iya kula da ita a can din ma” Shiru yai few minutes kamar ba zai ce komai ba, sai kuma yai maganar cike da gundira kamar wanda ya shekara yana magana da wani. “Yeah ita ce ta ki ta yarda wai ta fi son kusa da Familyn ta har sai ta ji sauki sosai sannan ta koma” “Amman ai zaka iya convince dinta ta yarda ta bika” Aliyu be sake ce masa komai ba, wayarsa da ke aljihu tai kara alamar sako, fiddo wayar yai ya duba. _Na shirya kuma ina son ruwa_ Cikin sauri ya saka hannu ya mike tsaye yana kallon Nasir. “Matata tana da muhimmanci a gurina i can't choose my work over her, kar ka sake min irin wannan maganar” Yana fadar hakan ya jefar da takardun saman center table din dake tsakanin shi da Nasir din ya bi ta kofar ciki ya fito ta baban falon. Kai tsaye freezer ya nufa ya dauko robar ruwa ba mai sanyi sosai ba da cup ya nufi upstairs. Tana zaune bakin gado ta cancanda ado kamar wacce zata je gurin biki sa kanshim turare take. “Princess you look cute” Ya fada yana kokarin aje ruwan kasa tare da kai hancinsa ya shimshina gefen wuyanta. “Kun kare meeting din?” Ya gyada mata kai yana zuba ruwan a kofa. “Nasir ya tafi?” Ya daga kafadunsa alamar be sani ba, sannan ya kai mata ruwan a baki, kadan ta sha ta kawar da kai. “Mu tafi yanzu” Ta riga shi mikewa tsaye kamin shi ma ya mike ya riko hannunta suka sauko downstairs. Kadan kadan take tafiya kamar mai tausayin kasa har suka isa gaban motar ya bude mata ta shiga, ganin babu motar Nasir na tabbar masa da cewar ya fice. Front seat ta shiga shi kuma yaja motar tun kan ya juyo da motar mai gadin ya bude masa gate. Kai tsaye Family house dinsu Rahama ya fara isa ya aje, sai suka bude motar suka fito tare, tana gaba yana bayanta har suka shiga cikin falon yadda ta tararda fuskokin my siblings dinta ta san ba lafiya ba. “Miya faru na ga fuskokinku a haka?” Ta fada cike da faduwar gaba, tana kokarin zama kusa da kanwarta Razinatu. “Wallahi one of those big shopping mall din Daddy da ke kano ya kone, ya ma tafi can tun da safe shi da Mommy” “Innalillahi wa'inna ilaihirraji'u” “Saboda wannan tashin hankalin na ki yace kar a fada miki baya son ranki ya bace” Cewar Razinatu sannan ta shiga sahun yan'uwanta da ke mikawa Aliyu gaisuwa, shi kuma gaba daya hankalinsa yana kan Rahma ganin kamar ta tashi hankalinta sosai. “Dear” “I'm okay, idan ka je ka ce ina gaishe da Momy kuma na mata naganar mai aikin” Kai kawai ya gyada mata sannan ya juya ya fice wani shan kamshi. Yana shiga motarsa ya dauki hanyar family house dinsu daman yana jin cikinsa babu nauyi. Ko da ya shiga falon ya tarar Momy na tattara littafan da jikokinta suka watsar wato kanenen Aliyu da akaiwa aure suka haihu. “Momy barka da safe” “Safe yanzu 12:13pm?” Ta fada tana kallon katon agogo dake falon. Shi ma kallon tsadadden agogo hannunsa yai kana ya zauna yana fadin. “Ban san ta yi ba, gaske na ji cikina ba nauyi” “Matarka bata nan?” “Tare muka fito da ita na aje ta gidansu” Momy ta cigaba da tara books din ba tare da ta kara cewa komai ba, shi kuma yana ta kallo yanayinta. “Anything Momy?” Sai ta kalleshi. “No nothing kawai ina tunani ya kamata ace ka ci abinci ne kamin ka fito” “Momy yadda kike tunanin Rahma fa ba irin waennan 'ya'yan talakawa ba ne, duk wani aiki mai nauyi Rahma ba za ta iya ba, ko da can ma balle yanzu, kuma dacan Rahma tun da ta tashi a gidansu ba ta aikin komai bayan hutu saboda ciwon kidney din da take” “Kuma bata iya zuwa gidan sukukanta ta gaishe su ba ko? Gidansu kawai ta sani sai gidan kawaye sai fita waje idan ta gaji da kasar” Ya shafa kansa yana ta neman kalmomin da zai hada ya fahimtar da mahaifiyarsa ko wacece Rahma. “Yana da wahala ka ga kafar Rahma a gidan nan sai idan wani abun ake muhimmi, shin bata san zuwa gida sukurukai gaishesu yana da muhimmanci ba? Ko ta dauka Fulani ce Real Mother dinka? Bata taba fada mata cewar ni na haife ka ba? Ko kuma tana ganin kamar bana jin zafin abun ne? Idan zaku zo hutu daga Abuja wani lokacin har ku kuma ba zata tako kafarta gidan nan ba, sai idan za ku tafi shi ma idan kuna tare,, balle kuma ta dauko wani abu ta kawo min ko ta aiko min, ba dan ina da bukata ba, amman kowa yana son kyautatawa” Momy ta fada mishi with serious face. Mikewa yai tsaye ya nufi dinning ba tare da kalma daya ta sake fitowa daga bakinsa ba sai dai yadda yaga fuskar mahaifiyarsa ta cikinsa yasa shi jin babu dadi be taba daukar abun nan da Rahma take wani abu ba, a ganinsa Rahma ta riga ta saba da rayuwar turai ne, ita kuma Momy ta kasa hakan, ba kamar Mama Fulani ba da bata taba damuwa da shiga safgar Rahma ko da kuwa zata taka ta ta wuce ba dan komai ba sai dan tana ganin daga Rahma har ubanta ba su kai matsayin da zata iya kallonsu ba, domin ita bata huldu da duk wani mai kudin da baya isa amsa sunansa a birnin Abuja. ____________ Assalamu Alaikum. Kwana biyu ban yi posting ba hakan ya faru ne saboda rashin lafiyar Kakata, amman yanzu Alhamdulillah, In-Sha-Allah posting babu kama hannun yaro. And ina son nai amfani da wannan damar na sanar da ku cewar da zarar mun kai page 12 za mu tsayar da Free pages, hakan na nufi sai mutum ya biya sannam ya samu cigaban labarin, daman na fada tun a ZABIN RAI cewar littafin ZAKI na kudi ne, wadanda suka sani sun sani domin na fada, and ina yin littafi free, wanda zai zo bayan shi na kudi, kamar dai yadda RAI BIYU ya zo free HAFSATU MANGA (yarinyar K'auye) na kudi, haka ma ZABIN RAI free ZAKI na kudi. Ga wanda suke son fara biya tun yanzu za su iya turo 300 to 0314795884 Abubakar Hadiza Gt Bank. sai ku turo shaidar biyan wato screenshot ta wannan number 08036126660, 'yan nijar za ku tura 500f na line orange ko zain ta number nan +22790165991 sai ku min magana ta wannan number 08036126660 Za'a saka ku Paid Group. Thanks 🙏🏻 https://my.w.tt/PWohUhlPv9. *Z A K I* By Khadeeja Candy 1️⃣0️⃣ Kamar wata mahaukaciya haka na rika ratsa mutane ina cusa kaina har na karasa inda yake, ihu yake ta yi yana rike da jafarsa yana jiran sunana. “Wayyo Allah Ataa kafana wayyo ni kafana” Babu jini a kafar amman yadda yake ihu cikin magagi ya fahimtar da ni irin ciwon da kafar take masa, ga gefen kansa sai jini yake yana ta wani jujjuya ido kamar zai shude. “Ai wallahi Allah ya kara mutanen ba su da godiyar Allah, kullum cikin bara, da sun hango mota har sauri suke su mikawa mutane hannu, yara kanana an koya musu bara” Shine abunda mafi akasin mutanen da suke gurin suke fada, masu ganin tausayinsa kadan domin sauran ta'alaka abun ne da rashin wadatar zuci irin na mu, na raba a titi da kaskantarta kai. “Jama'a ku taimaka min kar ya mutu” Shine abunda ya iya fada cikin kuka, sai daya daga cikin mutanen da ke tsaye ya zo ya dauke shi ya saka a mota wanda na ke kyautata zaton shi ya kade shi. Gidan baya ya bude min na shiga gurin da Lukman yake sannan ya bude mazaunin direba ya zauna na fisgi motar muka doshi specialist hospital wato asibitin daji. Muka isa aka wuce da shi layin yan hadari ni kuma na bi bayansu hankalina a tashe, sai da suka fada min cewar na je na karbo kati na tuna da kudin da suke hannu, ba ko tantama sun fadi tun a lokacin da hadarin ya afku, da sauri na fita emergency din zuwa neman mutumen ko zan ganshi ya taimaka min, sai na nemesa na rasa, wata kila shi kuma ya tafiyarsa. Komawa nai ciki ina rokonsu su taimaka su kula da shi kamin na kawo kudi sai suka ce min wai sai na zo da police za su iya taba shi, haka suka kyale Lukman a wulakance cikin gurin da duban mutane suke sai ihu yake. Ji nai kamar na je na dauke shi nai tafiyata idan kuma na dauke shi ban san inda zan kai shi ba, ba ni da wani magani da zan iya masa. Tasowa nai na fito daga cikin gurin ina tafiya hawaye masu zafi suna sauko min, yanzu yan kudin da suka rage min da kuma wadanda mukai bara muka samu na zubar saboda kidima, ga shi Lukman ya bugu da mota ga Nana tana asibiti tana jiran na kawo kudin maganin da hoto. Wani abu na ji ya tsaya min a zuciya yana neman numfashina, a take tsayuwa ta gagareni, ba zan iya fadar inda na ke ba, iyakar abunda na sani na ji na zauna saman wani abu mai kamar kaya, sai kuma duhu ya rufe min ido har na soma jin kamar babu sauran numfashi a tare da ni. Ban san iya awanin ko mintuna dana dauka a gurin ba, kamar wacce aka sakowa numfashi daga sama haka na farka firgigit ina maida numfashin wahala, baren kaina na ji yana min ciwo, gurin da na ke zaune sai sukana ake, hakan yasa na unkura na tashi tsaye sai na lura ashe saman fulawoyin na ke zaune masu kaya, da na soma tafiya sai na ji jiri na ďibata idanuwana kuma suna ta lumshewa kamar mai jin bachi. Haka na fito bakin gate din asibitin ina tafiya kamar marar lafiya, bakin titi na tsaya na tari wani mai Napep yana tare da wata mace a baya, yana tsawa na duka har kasa na hade hannayena ina rokonsa. “Dan Allah ka taimaka min ba, kanene yai hadari mutumen daya kawo shi asibiti ya gudu ya bar mu, su kuma sun ce baza su duba shi ba sai na kawo police kuma ba ni ko kudin siyen kati” “Yanzu me kike so?” Matar da ke baya ta fada tana dage nikab din dake fuskarta. “So na ke ka taimaka min na dauko shi na saka a ciki na kai shi gida” “Innalillahi wa'inna ilaihirraji'u, mutane suna ciki hali, ke yanzu kudin Napep din ma ya gagara? Allah ka ba mu karfi da ikon da za mu iya taimakon bayinka marasa shi” Ta fada tana miko min dubu daya yan dari biyu guda biyar, sannan ya ciro dari biyu ta mikawa mai Napep din. “Je ka kaita ni zan tari wata na shiga” “Na gode Allah ya saka miki da alheri” Tana fita na shiga zauna a ciki mai Napep din ya janyo ta ciki muka shiga har bakin kofar emergency. Da sauri na fita daga napep din na shiga ciki sai na same shi a inda na barshi, sai dai baya motsi babu alamar numfashi a tare da shi. “Kun kasheshi, kun bar shi nan ba ku taimaka masa ba, ya mutu kun ji dadi” Shine abunda na fada ina kallon nurses din ina hawaye kamar ba gobe, sannan na duka na saka hannuna biyu na tallabo shi na juyo na fito da shi mai Napep din ya taimaka min ya saka shi a ciki ni kuma na shiga, ina ta shafa fuskarsa ko zai farka amman shiru, can na kai hannuna gurin hancinsa sai na ji babu numfashi ba alamunsa. Har muka isa Clapperto road kuka kawai na ke ina rike da Lukman, mai Napep din ne ya fito ya saka hannunsa ya dauko shi ya kai shi gurin da na nuna nasa wato cikin kangon gidan nan ya aje min shi sannan na saka hannunsa aljihu ya ciro dari biyar ya miko min. “Gashi ku kara Allah ya muku mafita” “Na gode” Na Fada cikin muryar kuka. Sai ya juya cike da tausayawa ya fice, ni kuma na zauna a gurin ina ta kallon Lukman wai ko zai motsa amman shi, har hannuna na kai na dan matsa gurin kafar inda na ga yana riko dazun ko zai motsa amman shiru. Kaina na daga saman ina hawaye cikin daga murya irin da masu neman dauki nan cikin gaggawa na ce. “Allah kai ka so haka a garemu, komai ya samemu da saninka ne da yardarka, Allah ka sani ba ni da wata mafita sai ta ka, Allah kana ganin halin da na ke ciki Allah ka kawo min dauki” Sannan na tashi na je nai alwala nayi Sallah, ban tashi daga gurin ba, sai da na gabatar da sallah la'asar, sannan na mike tsaye ina murza kudin da ke hannuna zuciyata sai wani abu take min babu dadi, da kafa na taka zuwa asibitin uduth wannan karon babu masu gadin dakunan kasancewar la'asar, cike da nauyin kafa na ke taka ward din ina sakesaken abunda zan fadawa Nana, idan ma na boye mata dole zata san gaskiya, idan kuma na fada mata zata iya shiga wani hali sai na kasa za6a tsakanin fada mata da kuma akasin haka. Kwance na sameta ba kamar dazun da na bar ta jingine ba, ban san hawaye na min zuba ba har sai da ta nuna fuskar tawa. “Miya saka kike kuka Ataa? Wani abun ya samu Lukman ne?” Saurin share hawayen nai ina girgiza mata kai. “Aa babu abunda ya same shi” “Karki boye min, fada min babu abunda zan iya da lamarin Allah” “Mota ta kade shi Nana, kuma an kai shi asibiti amman baya motsi na dauko shi na dawo da shi gida, kuma kudin da na samu da ragowar duka sun fadi” Kamar wacce aka yi ma allurar karfi da kuzari, haka ta tashi zaune kamar ba ita ba. “Lukman din ya mutu ko?” “Ban sani ba amman dai baya numfashi kuma yai ta ihu lokacin da aka kade shi ya rike kafarsa yana da kuka sosai” “Innalillahi wa'inna ilaihirraji'u ” Ta fada tana mikewa tsaye har mamaki ta bani dan zaka rantse da Allah cewar ba ita ce ke kwance malala dazun ba. “Mu tafi” Ta fada tana jan dayan zanen da ke saman gadon ta rufe jikinta. Ni kuma nai saurin rikata n zaunar. “Ba za su bari mu tafi ba sai mun biya kudin gado Nana, ki zauna zan je samo wasu kudin na biyasu sai mu koma gida” Zaunawa tai a saman gadon sai ta fashe da wani irin kuka mai taba zuciya. Ni kuma nai saurin fita daga gurin ina sauri kamar zan halde kafafun. Lokacin da na fito bakin kofar asibitin sai na rasa abunda zan yi, wace hanya zan bi na samu kudi? Baran zan sake komawa ko kuwa sata zanje na yi ko mutuncina zan siyar, idan ma sata zan yi ina kudin suke da har zan sata? Ina mai siyen mutuncin yake da har zai siya, a nawa zai siya, mi zai biyo bayan wannan? Wani tunanin ya zo min, da sauri ma tari Napep na shiga na ce ya kaini ofishin yan sanda, yana tafe gabana na faduwa abunda da wacce ba ta saba ba, musamman a lokacin dana sauka daga Napep din na doshi cikin ofishin, sai bugun gabana ya karu ina jin kamar ba zan iya ba, ganin irin manyan bingogin da suke rike da su. A haka dai na daure na shiga gurin ina sallama muryata na rawa kamar mai jin sanyi. “As..sa.. La.mu...Alai..kum.” Mutum biyu suka amsa min, sauran kuma suna ta kula da wasu mutane da ke kusa da su suna musu wani complain din dabam. “Wa kike nema?” Wani mai babban muryar ya tambaya yana kallon yanayina. “Karar wani likita na kawo” “Likita kuma? Me yai miki?” “Kodar mahaifiyata ya cire, ba tare da saninmu ba, kuma ni ban ce ya cire mata ba” Na fada ina kuka. Sai daya daga cikinsu ya zaro ido. “What...?” Sai dayan ya ce. “Koda? Babbar magana, Robot bude nata file ka dauki statement dinta” A take na zayyana musu komai yadda ya faru cikin har da maganin da ya bani da kuma abinci, sannan na fadi yadda wacan likitan na uduth ya fada min. “Amman ke ai ba ki da shaida” “Amman ai hoton ya nuna bata da koda kamar yadda likitan ya fada, kuma ashe ba ayi ma dafin maciji tiyati ni ban sani ba” Cikin kuka nake wannan maganar ina share majina da Hijab dina. “Dan Allah ku taimaka min ku kawto min hakkin mahaifiyata, yanzu haka tana asibiti babu kudin jinya sakamakon kodar nan da ya cire mata” “Kin san inda likitan ya ke?” “Ban sani ba, amman na san asibitinsa kuma can yake aiki kusan ma can yake zama kullum” “To yanzu kin san yadda za ayi kina da na mai?” Na mika masa dubu da dari biyar din da ke hannuna. “Wannan kudin ne kawai ban sani ba ko za su isa” Daya daga cikinsu ya karba sannan ya zagayo tare da wasu polisawan uku suka fito daga ofishin, sai da suka janyo motar yan sanda suka ce da ni na zo na shiga na nuna inda yake, cikin kuzari na shiga motar ina ta jindadi da ganin kamar za su kwato min hakkina ne, ashe ban sani ba gwanwo ne zai juye da mujiya. _______________ Ayi hakuri na yau be kai yawan na kullum ba, gobe zan cika In-Sha-Allah. https://my.w.tt/PWohUhlPv9. *Z A K I* By Khadeeja Candy 1️⃣1️⃣ “Momy muna neman mai aiki wacce zata rika gyara mana gida” Ya fada yana aunar jalof din taliya da Momy ta zuba masa. “Yar talakawa za'a nemo maka kenan, kaga ko dan za a ci amfaninta” “Za tai ci amfaninmu ai biyanta za a yi” Momy ta yi murmushi. “Dan wajen Fulani har yanzu ka ki yarda da cewar za ka ci ribar talaka ko?” “Momy kece ai kin ji ki gane, idan ba wani abu zaka saka talaka ba ka biya shi me zai hada ka da shi, Mama Fulani tana yawan yi min bitar kar na yarda ko rigata talaka ya rika balle kuma har ta kai ga alaka, kin san talaka dan hassada ne” “Lallai kuwa, ina jiye maka tsoron ranar da zaka fara kaunar talaka, wata kila abun ba zai zo maka da sauki ba” “Kamar ya?” “Ba a son fariya, Allah zai iya jarrabarka ya koma talakan cikin talakawa, ko kuma Allah ya jarrabe ka da son yar talakawa wacce zaka duka har kasa kana rokon ta so ka?” Ya tofar da ragowar abincin da ke bakinsa. “Allah ya tsare ni Momy, ni ai bana da ra'ayin mace fiye da daya, Rahma ce kawai bayan ita babu wata” “Wallahi yayan talakawan nan akwai tarbiya, da ace Rahma yar talakawa ce da zata fi ganin girma da girmanka fiye da yanzun” “Ko a yanzu tana ganin girman ki Momy, kawai dai ita ta tashi a rayuwar turai ne, kuma kin san irin Rahma bata tashi gidan wahala ba shiyasa....” “Hmmm To Allah ya kyauta” Shine abunda Momy ta fada daga karshe sannan ta tashi daga dinning din ta nufi kitchen. Sai bayan sallah magariba ya biya gidan family house dinsu Rahma ya dauko matarsa suka dawo gida. Kamar wata marar lafiya haka ta shigo cikin falon tana takawa kamar mai jin wahalar tafiyar. “Wani abun ne Dear?” “Aa Daddy be dawo ba, kuma ance yai hasara kudi da yawa a shopping mall dinsa daya kone” “Shine kuma za ki dauki damuwar ki saka a ranki? Bayan kin san lalurarki?” Tai murmushi tana kai hannayenta ta zagaye wuyansa. “Ina kokarin kawarda damuwar fa ko dan saboda na rayu da kai” Kissing din lips dinta yai sai kuma ya rumgume ta a kirjinsa. “Ka yi Momy maganar mai aikin? Ni wallahi har kyamar shigowa dakin nan na ke, duk datti” Yai shiru be ce da ita komai ba. “Bathrooms din mu duka suna son gyara fa, ga tarin wanke-wanke, ga kitchen din mu and bedrooms duka datti, ko mopping an dade ba ayi ba, kuma kasan ba zan iya ba” “Shiiiiiiiii” Ya fada yana shafa bayanta, yasanta da  yawan magana wani lokacin kamar radio, ga shi kuma baya son yawan magana sai idan da Mama Fulani ne ko Momy. “Doc Asim zai rika zuwa yana duba ki kullum” Ya fada bayan ya saketa, sannan na nufi upstairs. ATAA POV. Mun taki sa'a domin kuwa mun isa cikin asibitin a lokacin da yake tsaka da aiki, ina gaba polisawan ba bayana kowa sai kallon mu yake har muka isa ofishinsa, da muka shiga sai muka tarar baya ciki wai yana dakin tiyata, a ofishin mukai tsaye cirkocirko muna jiransa har ya fito daga dakin tiyatar ya shigo ofishin, da fari tsayawa yai yana kallon polisawan kamin ya maida dubansa a zuwa gareni, da alama an labarta masa zuwan mu tun kan ya shigo ofishin. “Kai ne Doc Asim?” Daya daga cikin yan sanda ya fada sai ya gyada masa kai. “Yes wani abun ne?” “You're Under arrest” “Akan me?” Ya tambaya kamar da gadara, ni kuma nai karfin halin bude bakina na ce. “Kai ka cirewa Mahaifiyata koda dan haka dole a kama ka kuma a kwato mata hakkinta” “Kodar da kika siyar? Blackmailing dina za ki yi? Are you out of your sense?” Mamakin furucinsa ya hanani ko da motsin kirki balle har na sake cewa wani abu, waina siyar da koda, yaushe na siyar? Wa na siyarwa ya ma za ayi na siyar da kodar mahaifiyata. “Oficer kar yarinyar tai wasa da hankalinku ta raina muku aiki, kar kuma ku isko ni har cikin ofishin ku ce za ku ci min mutumci akan aikin, muje station din ku hada da dan sanda ku daya zan saka shi motata sai mu tafi station din amman ni ba zan shiga motar ku ba” Yadda ya bukata haka akai, ni da sauran polisawan muka koma a motar da muka zo, shi kuma ya shiga motarsa da dayan dan sanda bayan ya dauki wasu takardu. A motar yan sanda sukai ta tambaya wai da gaskiya na siyar da kodar nai ta musu rantsuwar ban siyar ba, ban ma ya cire ba, idan har na siyar mi zai sa na kawo kararsa gurinsu, a nan suka min tausayawa kuma suka ce za su kwatar min hakkina, dan sanda yana ya matse ni sosai jikinsa na ta gogar nawa. “Yarinya kyakkyawa da ita za a ci amanarta, ki sha kuruminki sai mun kwato miki hakki” Shine abunda ya fada yana kallona da jajayen kamar dan shaye-shaye. A lokacin da muka isa Station din sai muka shiga ciki, a nan ya fiddo da wasu takardu ciki har da takardar da na sakawa hannu lokacin da za ayi ma Nana tiyata. “Kin san kin saka hannu a wannan takardar ko ba ki sani ba?” “Na saka” Na amsa masa ina kallon takardar. “Magani kawai na dubu nawa kika siya mata? Abincin da kike ci safe da rana da dare daga Hotel ake kawo miki duk ina kika samu kudin?” Kasa magana nai sai hawaye na ke gaba daya ya gama dauren kafafu kai har ma da jikin gaba daya. Sai kuma ya juya gurin polisawan ya ce. “Yi ma Babban likita irina sheri abu ne mai sauki domin ta samu kudi, yarinyar nan ina zaman ta dauko mahaifiyarta ta kawo wai maciji ya tsareta, kuma babu yadda zata yi ita bata da gabas bata da yamma, na ce ni ba zan taba ba, sai an kawo kudi, sai kawai ta ji ina magana da wani mai neman koda a nan tace zata siyar kuma babu yadda ban yi da ita ba akan ta nemo manyanta sai tace daga ita sai mahaifiyarta suke wai basu da kowa a nan, kuma idan ban taimaka na siye kodar mahaifiyarta ba, babu inda zata samo kudin da za ayi mata allurar dafin macijin, a haka tai convince dina na yarda na bata takarda ta saka hannu, na bata kudinta ta ce aa na aje gurina na siya mata magani ragowar canjin na bata wannan ne kawai abunda na sani” Cikin kuka na nuna shi da yatsa na ce . “Allah ya isa, karshenka ba zai yi kyau ba, kuma za ka ga abunda zai same ka?” “Kaji ko? Oficer nima bude min file sai na ji akan me take kokarin bata min suna” Ya fada yana nuna ni. A maimakon polisawan suyi wani abu sai na ga kamar suna tsoronsa, ashe ya siye dayan sandan daya shiga motarsa, sai kawai na ga sun fita waje har da shi Doc Asim din sun kebe suna ta magana da juna, suna kawowa sai suka fara tuhumata wai waya biyani na bata masa suna. “Babu wanda ya saka ni, amman wallahi karya ya fada” “Kina da wata shaida ne? ” “Ba ni da ita, amman Allah shine shaidata” “Aikin banza, haka kawai za ki nemi batawa mutum aiki da suna?” “Wallahi ba bata masa nai ba, gaskiya na fada” “Wannan duk shairin makiya ne, so kawai take ta bata min suna, dan haka su saka ta a cell sai ta fada muku wanda ya saka ta yin wannan sherin” Cewar Doc Asim cike da gadara. Ni ko ina jin haka sai tsoro ya kamani take na saka kuka, ni ce da gaskiyata amman na risina har kasa ina rokon Doc Asim yafiya, sai ya fisge kafarsa ya daka min hannu har sai da dan yatsana ya fashe saboda zafin takalmin kafarsa. Haka suka rika ni saboda tsabar zalince suka saka ni a cell din mata ina ta kuka kamar raina zai fita.   Daga cikin matan da ke cell din ta daka min tsawa wai na yi musu shiru na cika musu kunne da hayaniya, a haka nai shiru na samu guri na rabe a cikin dakin mai cike da sauro da duhu sai wari yake.    Ba a bari ka fito ko da sallah za kai, fitsari ma sai dai kai a cikin cell din gaban kowa da kowa. Dukan tunani sai ya karkarta gurin Nana ban san halin da take ciki ba, ban san iya tsawon lokacin da zan dauka a nan ba. Da dare yai sai naga ana fita da mata masu kyau, can da asuba kuma aka kawo su, ni dai ina zaune jigum har safe ban saka komai a bakina ba, sai can da azahar wani dan sanda ya bude min yace na fito a nan na samu damar yin alwala na raba gafen masallacin mazan nai rama sallah da akd bina sannan na gabatar da azahar, a lokacin ne dan sanda ya kawo min abincin shimkafa da miya har da kabeji da nama, kadan na ci saboda cikina ya daure sosai bayan na gama ya bani ruwa mai sanyi na sha. “Idan an jima da dare zan zo na dauke ki, sai mu fita mu sha iska, idan mun dawo zan yi belinki da safe kin ji” Na gyada masa kai cike da fahimtar inda manufarsa ta dosa, ba sai ya fada min na fahimci dan iska ne, ashe abunda suke da matan da suke fita dasu da dare kenan. Yadda ya fada haka ya nufoto ni da dare guraren karfe goma sha biyu ya bude cell din wai na fito, ni ko na ki yarda na fito din, da ya shigo ya jani da karfi sai na fasa masa kuka ina ta masa ihu kamar zai sace ni a dole ta saka ya kyaleni yai tafiyarsa. A haka na kwana hudu a cikin cell babu wanda ya zo belina, abinci kuwa sai idan polisawan sun ci sun rage su ba ni raguwar ko kuma mutane za da ke cell din idan an kawo musu sun ci sun koshi sai su ba ni ragowar. A cikin kwana biyu Allah ya hada jinina da daya daga cikin yan matan cell din, na dauke ta kamar yaya ita kuma ta rike ni tamkar kanwarta kasancewar ta girme ni nesa ba kusa ba. Bata fada min dalilinta na zuwa cell din ba amman na fahimci kamar shaye-shaye take har aka kawo ta nan, da fira tai mana dadi take tambayata dalilin zuwana gurin na fada mata sai ta tausaya min sosai. Ita ce ta taimaka min ta fitar da ni daga cell a lokacin da aka zo belinta sai akai belinmu mu biyu ni da ita. Ranar da na fito daga cell din har iskar sai na ji ta badan ina ra jina kamar mai hanci, abu ga marasa shi, daga station din zuwa uduth akwai dan karen nisa amman haka na taka da kafa idan na gaji sai na tsaya na hutu har na isa cikin asibitin, ban san time din da na isa ba, sai dai da naje sai suka hanani shiga, a gurin na zauna har hudu tai sannan na shiga ciki, gurin da na san na bar Nana na nufa sai na samu babu ita a gurin gadon ma har an dora wata, ban tambayi kowa ina take ba na juyo na kamo hanyar Clapperto ina kuka. A iya tunani Nana ta rasu, idan ma ta rasu ina suka kai gawarta? Kangon gidan na nufo sai na tarar an saka kwano an zagaye shi an rufe ruf ba ta inda mutum zai iya shiga, a gurin na zauna nai ta rare kukana sai da nai mai isata, ban dauki wannan abun komai ba, face kaddara da kuma jarabawar rayuwa wacce ko waji dan adam yake fuskanta sai dai kowa da irin tasa, amman a iya ganina da jina ban tana ganin wanda ya shiga matsanaiciyar rayuwar da na shiga ba, kullum abun gaba yake ba baya ba, idan na natsu ina tunani sai na ga ban kashe kowa ba, ban hada Allah da wani ba, amman abubuwan da suke faruwa da ni kamar na kauce hanya ne, wata kila akwai wani abun da na ke ba daidai shiyasa Allah yake jarrabani, kuka nai mai isa ta sannan na tashi na doshi gidansu kawata Farida. Ina shiga ta yo kaina da gudu ta dafani. “Ataa ina kika shiga? Mi ya same ki wannan irin ramar fa? Duk kin yi baki kamar ba ke ba” Kasa amsa mata nai sai kawai na fashe da kuka. “Ataa ina kika shiga? Hankali Nana duk ya tashi kullum zancen ki take” “Nana tana nan?” “Gata a can” Ta nuna min wani tsohon kitchen dinsu, da gudu na nufi kitchen din ina shiga na samu Nana kwance sai kawai na fada jikinta na fashe da sabon kuka na rumgumeta kankan ina jin kamar wani zai rabani da ita. Ita kukan take ni da ita sai aka rasa mai rarrashi wani, Farida ma da ke tsaye jikin kofa tana kallon mu kuka take. “Haba Ataa ke kuka ita kuka sai ki saka zuciyarta rauni ai” Maganar Farida ce tasa na tsagaita kukana na share hawayena ita na saka hannuna na share mata hawayenta. Ta rame sosai wata kila ko abinci bata samu sosai ya akai ma ta bar asibitin ta dawo nan? Ganin na daina kukan yasa Farida ta fita ta bar ni daga ni sai Nana. “Nana ina Lukman?” “Yana gidansa na gaskiya, sai idan Allah ya hada mu” Wani sabon kuka na ji na cika min ido, sai tausayinta da shakuwarta da Lukman ta rufe ni, daman daga ni sai ita sai Lukman muka rage, yanzu kuma ya tafi ya bar mu mu biyu kawai. “Ina kika je Ataa” “Karar wannan likitan na kai gurin yan sanda akan rashin kula da ke da yai da kyau, sai ya juyar da abun a kaina suka rufe a cell sai da wata mata ta fitar da ni” “Ranar da kika bar ni ban iya kwana cikin asibitin nan ba, sai na saci kafa da suna zuwa bandaki na gudo na dawo gida, a nan na tararda gawar dana, na nemi taimakon mutane akai masa wanka aka siya masa likkafai akai masa sallah aka je makabarta aka binnesa, a ranar mai gidan nan ya turo aka kore mu, da safe ana kewaye masa gurinsa dan kar mu sake zama, Farida ce tasa muka dawo nan ta ba ni kitchen dinsu na zauna a nan nake ta rayuwa da tunaninki, na dauka ma ke ma kin mutu kin bar ni ni kadai” Na kama hannunta hawaye na min zuba kamar yadda ita suke mata zuba. “Ban mutu ba Nana, kuma ba zan tafi na barki ba, kuma In-Sha-Allah za ki samu lafiya sosai, zan nema miki magani In-Sha-Allahu” “Aa ba sai kin nema min magani ba, dawainiyar da kikai da ni ma Allah ya miki albarka, da kuciyarki kin fada cikin wata rayuwa mai tsananin wahala da sarkakiya, kina fuskantar kalubale kala kala na rayuwa” “Idan ban nema miki lafiya Nana wa zan nemawa? Ba ni da wani wanda ya fiki a gurina, ganinki kawai yana sani kwanciyar hankali” Dan murmushi tai sai ta koma ta kishingida da alama har yanzu lafiyar bata wadace ba, taya ma zata wadace bayan ba a nema mata magani ba, ba a mata maganin daya dace ta sha ba. Babu abunda ke zuciyata sai Allah ya isa da na ke yi ma azzalumi likitan marar imani da tausayi. A gurin muka kwana ni da ita cikin matsuwa domin ba kitchen mai fadi ba, gashi duk ya kone saboda girkin da akai cikinsa can baya kamin su daina girki ciki, da dare Farida ta kawo mana abinci da alama ma tuwonta ne wanda zata ci ta kawo mana, dan nasan mahaifiyarta ba zata taba dauka tuwo ta ba mu ba, balle yadda ake fama da tsadar rayuwar nan. Bayan mun gama sallah asuba, Nana ta koma bachi, ni kuma na daddaka gawayin da na shafa a fuskata, na yafa hijabina na fito ba tare da sanin kowa ba, da kafa na taka har unguwar Nasarawa, babban unguwa ce ta manyan masu kudi da yan siyasa gida gida na soma shiga ina tambayar aiki, a ganina samun aikin zai fi min bara, domin bana sha'awar baran tun da na rasa dan'uwana Lukman, amman aikin zan iya samun abinci har na kawo wa Nana. A haka har na fada wani babban gida mai cike da fulawoyi da manyan motoci, da fari mai gadin gidan hana ni shiga yai, bayan na juyo sai kuma na ji ya kirani. “Ke zo ana kiranki” Da sauri na dawo na shiga cikin gidan, shi ya nuna min kofar har na isa gaban kofar na tsaya ina ta kallon inda mutane za su fito. Zuwa can na ga wata mace ta fito wacce kudi da jindadi da rayuwar hutu suka gama bayyana kansu a jikinta. Tana kallona sai ta ya mutsa fuska. “Me kike so?” “Aiki” Na Fada da sauri, sai ta kalli sama da kasa ta dan tabe baki ta juya cikin falon kamar tana magana da wani, bayan yan mintuna mutumen da na taba fasawa mota kuma mutumen da ya taba jefar da rigarsa saboda na taba shi ya fito cikin farar shadda riga da wando, fuskarsa kamar ta ranar nan babu yabo ba fallasa, sai kwarjini da haifa, kallo daya nai masa na sadda kaina kasa, yau kan ban ji tsoronsa kamar yadda na saba ji ba, wata kila saboda uzurin da ke gaba ne, ko kuma dan na kawo kaina a gidansa ne. “Look at her face, wannan ai ta cika kazanta” Yai magana kamar ba shi ba, ashe dai yana magana mai sauti har ta fito haka. Cikin sauri da rawar jiki na ce. “Zan wanke wallahi zan gyara ko a nan aka ba ni ruwa wankewa zan yi” “Nawa ake biyanki a wata?” “Ban taba yin aiki ba” “Ba ki taba ba?” Matar ta tambaya tana kwantawa jikin mijin na ta, shi kuma ya rumgume yana mata magana kadan-kadan, ban san mi ya ce mata ba sai naga ta dago ta kalleni. “Zan a baki dubu 8000 a wata hakan ya miki?” “Ya min amman ina rokon ki fara bani kudin yanzu” “Saboda mi? Kin taba ganin inda akai haka?” “Mahaifiyata bata da lafiya, ina son na siya mata magani da abinci, ni kuma na miki alkawarin yin aikin har wata ya kare” “Na baki kudi ki gudu?” “Kin fi karfin dubu takwas Hajiya, kuma ni miye ribata idan kin ba ni kudin na gudu? Idan ban miki aikin ba, zan biyaki kudin a lahira, mahaifiyata ce bata jindadi ki taimaka min da girman Allah” Na fada cikin roko da neman alfarma, amman matar nan ta murje ido ta ce ita bata yarda ba, ba za ta ba ni kudi na gudu ba. “Ina ne gidanku ina iyayenki suke?” Na kwatanta mata tare da fada mata cewar ba mu da gida wani guri ne mike rabe. “Dear Za mu bata kudin, lafiya tana da muhimmanci sosai, naga hakan tun a kan ki, idan ta gudu da kudin ta yi wa kanta” Mijinta ne yai wannan maganar yana yana shafa bayanta, da alama yana son matarsa sosai. Ita kuma ta lake kafada wai bata yarda ba, ita ba za a bani kudin ba. “Aa zata iya guduwa da su, baka san halin irin mabaratan nan ba, idan kin shirya ki shigo ciki ki fara aikin” Tana fadar hakan ta juya ya shige ciki, ni kuma na tako dan stairs din da ke gurin da zimmar shiga ciki sai kuma nai tsaye ganin yadda mijinta ya tsaya a kofar yana ta min kallon kyama. “Ki koma gida ki wanke wannan bakin na fuskarka ki and make sure kin canja kayanki kin yi wanka kin fito fresh sannan ki dawo aikin nan” Ya fada yana jefo min kudin da nake saka ran sun fi dubu takwas din ya juya ya shigewarsa, ni kuma na duka da sauri na kwashi yan dari biyar biyar din jikina har rawa yake... *Z A K I* By Khadeeja Candy 1️⃣2️⃣ Kamar wacce akai wa kyauta makka yana na nufo gida farinciki ya cika min zuciya. Ina tafe fuskarta dauke da murmushi duk wanda ya kalleni ya san ina cikin farinciki a yau. Sallamar shiga gidansu Farida ma da karfi nai ta Mahaifiyar Farida na tsakar gida zaune tana gyara Alayyahu har kasa na risina na gaishe ta sai ta masa sama-sama sannan ta bawa banza ajiyata ni kuma na tashi na nufi kitchen da Nana take. Kwance na same ta kamar yadda na fita na barta. Kusa da ita na zauna ina washe hakora. “Nana na samo kudi har dubu takwas” Dan dagowa tai ta kalleni cike da mamaki. “Ina kika kudi har haka, bara ki kai?” “A'a ai ba zan sake yin bara ba, sanadin raban nan aka kade Lukman, bana ma marmarin sake komawa bara, wani gida naje na ce musu zan yi musu aiki, amman sai sun fara bani kudi sannan na fara, na fada musu cewar Mahaifiyata bata da lafiya” “Kuma suka yarda suka ba ki?” “Matar ba ta yarda ba, mijin ne ya ba ni” Hannu ta shafa kaina tana murmushi. “Allah ya miki albarka, wannan kalubale da kika fuskata tun a yanzu da kurciyarki Allah ya tallafa miki ya baki wanda zai mutunta ki ya zame miki gata” Kasa amsawa nai a fili saboda kunya, sai a zuciyata na amsa da Amin. “Nana ina takardar msganin take sai naje na siyo” “Ban zo da takardar ba, komai a can ya bar asibiti” “Kai amman ban jidadi ba, yanzu ya zamu yi kenan?” “Ataa ki daina dorawa kanki damuwa da wahalar da kanki a kaina” “Idan ban miki ba wa zan yi ma, ba ni da kowa a yanzu sai ke, idan na rasa ki ban san iya halin da zan shiga ba” Na fada idona tab da hawaye. Sai tai murmushi tana ta kallona cike da kauna. “Ko asibintin za mu koma?” “Asibiti babu komai sai cin kudi, kara ma kije gurin masu magani ki siyo abunda ya sawwaka, sauran kudin ki siyo mana abinci da su” “Amman maganin chemist anya zai yi kuwa?Ai kara dai mu koma asibintin zai fi” “Ataa na gaji da zaman asibitin nan, kuma wannan kudin idan ma muje karewa zai yi” “Ko ya kare indai kin samu lafiya ba matsala ba ne” “Aa kara dai mu ci abinci da su zai fi mana” “Amman Nana rashin sha maganin zai iya janyo miki matsala fa” “Da muje a kashe kudin ba a samu biyan bukata ba kara dai mu san mun saka a ciki, tun da kika fita ba ki ci komai ba, ni ma da nake nan ban cin ba, magani ma ai ba yayi sai da abinci” Gaskiya ta fada, sai dai ni na fi damuwa da ciwonta fiye da abincin, na san kudin ba zai isa maganin duka ba. Ta shi nai na fita daga dakin cikin rashin jindadin duk farinciki da murnar da na ke sai suka koma ciki.   Wani shagon provision na nufa na siyo mata biredi da madara da gwangwanin suga, ni kuma na siyo ma kaina gari da gida da suga sannan na dawo gidan, wannan karon Maman Farida ba tsakar gidan, hakan yasa ni jindadin wucewa na shigewa inda Nana ta ke na mika mata ledar sannan na fito da dauki kofi biyu da ruwa na koma dakin, ita na fara hadawa da ruwan sanye sannan ni kuma na hada nawa garin na saka suga na sha, yadda take fisgar biredin tana sai ka rantse da Allah ta shekara bata ci abinci ba. Tausayinta ne ya lullube, an cire mata koda daya dan zalinci, ga yunwa tana fama da ita babu mai bata sai Allah, dan ya tafi ya barta a garin nema yafiyarta. Tabbas ba zan taba manta Doc Asim ba, ba kuma zan taba yafe masa ba, sanadinsa na kwana a cell, na rasa kanena, ga mahaifiyata a halin da ba zan iya juye ganinta a haka ba. Idan zan yi tunani sai na rasa da wanne zan fara abubuwan duniya sun taru sun min tsaye a raina, har wani zafi na ke jin kirjina yana yi idan ina tunani, na rika jin zuciyata kamar zata fasa kirjina ta fito.   Bayan mun gama na dauki kofunan na kai waje na wanke na aje mata a inda na gansu, ashe ta hangi lokacin da na aje sai ganinta nai ta fito rai a bace tana ta masifa wai mun taba mata kofi kazamai da mu, a kan idona ta dauki kofunan ta wilgar bayan gidan, na ji zafi sosai amman ban nuna mata ba, domin fadanta akan gaskiya ne, ni na taba mata abu da ban taba ba da bata min wannan maganar ba.   Kitchen da muka raba na koma na dauko duka kayan wanke wanken na fito da su tsakar gidan, na je na siyo omo na debo ruwa a rijiyar gidan na zauna na wake su tas, na dauka na kai kitchen din wanda zan iya cewa dakinmu. Sannan na fito rike da soson wankanmu na dibi ruwan a robarmu na shiga bandakin tsakar gidan nai wanka, na wanka jiki sau uku sannan na saka ruwa na dauraye na fito fes da ni ni kaina har wata ni'ima na ke jin tana shiga jikina. Ban ssmu na shafa mai ba saboda yanayin garin da zafi, sai kawai na saka daya daga cikin tufafin da na ke ji da su, na dauki bakin dankwalina nai nikab da shi sannan na saka Hijab sama na duka inda kudin sukd na dauki naira dari na dan hawan acha6a, domin akwai tazara a tsakanin unguwar mu da tasu. “Nana zan tafi” “Yau za ki fara aikin?” “To Allah ya taimaka ya tsare a dawo lafiya” “Amin, ki aje wannan kudin muna cin abinci da su, idan na samu wasu wadanda suka yarda nai aikin yamma sai na rika zuwa ina musu kin ga idan an ban kudi sai na hada da wannan mu koma asibitin” “To Allah ya nufa” Duk maganar da nai mata da hausa nai ta ita kuma sa ta maida min da yaren da tafi kwarewa akai wato buzanci. Sai da nai mata sallama sannan na fita, ban yi nisa sosai na samu mashin na tara na hau yana sauke ni na bashi hansi ya karba ya wuce ni kuma na buga kofar gate din a hankali. Mai gadin ne ya leko yana ganina sai ya fito gaba daya. “Baiwar Allah lafiya” “Lafiya kalau, ni ce wacce na zo neman aiki dazu kuma suka ce sun dauke amman sai naje na shirya” Wani kallo yai min tun daga sama na har kasa, nasan kallon baya rasa nasaba da bakin kyallen da na saka na rufe fuskata, wata kila yana munanamin zato ne. “Bari dai na fara fada musu tukuna” Haka ya barni tsaye a gurin ya koma ciki, ba dauki dogon lokaci ba sai gashi ya dawo ya bude min gate din. “Ance kin shigo” “Na gode” Na fada ina saka kafata cikin gidan, sai a yanzu ne nake kara kare masa kallo babban gida ne da za ayi iya kiransa da aljannar duniya, ko a harabar gidan kadai aka barka zaka sha kallo tun daga kan furanni da kuma manyan motocin da ke gidan, ko wace kofa an kawata ta da furanni. A inda na naga sun fito dazun na na bi stairs din na isa gaban katuwar kofar mai kyau na yi knocked a hankali, shiru ban ji an bude kofar ba, hakan yasa na sake knocked, nan ma shiru ba a bude min ba, sai da na yi na ukun sannan aka soma motsa kofar aka bude. Mijin matar ne ya bude min yana sanye da kananan kayan, bakin wando da jar t-shirt, fukarsa kamar ta kullum babu alamar murmushi ma balle kuma ayi zancen dariya. “Ina wuni” Be amsa min ba, sai kallon fuskata yake kamar nai son tantace abu, ni kuma nai tsaye a gurin cike da tsawalla, gabana sai faduwa yake ina jin kamar cewa zai yi ya fasa baya so. Sakin kofar yai ya juya ya koma ciki ya barni a gurin tsaye shi be cena shigo ba, kuma be ce min na tafi ba, ganin hakan yasa na yi tsaye agurin kamar an dasani, har sai da na ji muryar matar tana ce min na shigo. Kamar wata hawainiya haka na rika taka tile din mai tsantsi gudun kar na taba da karfi su ce na musu ba daidai. A kan wata babban kujera suke zaune tun na shigo falon daga ita har shi babau wanda ya kalleni balle ya ce min wani abu. Haka ma zauna a gurin kamar daman sun biyana dan na zo na zauna gabansu ne. “Ke anya macen kwarai ce? Miyasa kika rufe fuskarki?” Matar ta fada tana min wani kallon uku saura kwata. “Ba komai, na fi jindadi idan na rufe fuskar ne shiyasa na rufe, ina da konuwa a fuskar ne” Ta tabe baki. “Bedrooms din mu za ki fara shiga ki gyara komai da nan falon sannan ki shiga kitchen ki gyara kuma ki wanke duka kayan da suke can sannan ki yi mopping ki saka mana turaren kanshi” “To ina dakunan suke?” Da yatsanta ta nuna inda yake har na mike tsaye sai kuma ya kira ni. “Keee ban da sata kar ki kuskura daukar mana wani a gida” “Ban taba sata ba a rayuwa” Na bata amsa cike da jin zafin furucinta. “And secondly mijina baya son kallo, kuma daga yanzu tun bakwai za ki rika zuwa kina hada mana breakfast, kuma ki gyara gidan, kuma kullum ki wanke mana bathrooms din mu” Tana fadar hakan sai na ga jikinta ya kalleta, ya kalli sannan ya sake kallonta. “Ban da girki, saboda shara da mopping kawai na dauke ta” Yana fadar hakan ya mike tsaye yana wani irin kamshi turare mai dadi shaka ya hau sama, ni kuma na maida hijab dina baya na daure sannan na nufi upstairs din na soma takawa a hankali kusa da sai na ce wannan shi ne karo na farko da na taba taka stairs bayan wanda na taka a asibitin uduth, dakin farko na fara kai hannuna na tura kofar dakin, da alama dakinta ne, domin kayan mata da ke dakin suna da yawa ga gadon duk an tumurmuza shi kamar karamin yaro ya kwana kai. Bedsheet din na fara gyarawa sannan na linke kayan kayan da aje guri daban, na duba iya dubana ban ga tsinsiya ba da abun mopping ba. Hakan yasa na fito na sauko kasa can nesa da ita na tsaya. “Ina tsintsiya?” “Ni zan dauko miki na kawo miki?” “Aa fada min za ki yi inda take na dauko” A gurin ta bar ni tsaye har na kusan minti ashirin sannan ta ce. “Tana can kofar baya ki je ki duba” “Ina ne kofar baya?” Sai da taja tsaki sannan ta bani amsa tana mikewa tsaye ta nufi upstairs. “Idan kin ga dama ki duba ta can” Inda ta nuna min na bi na je na bude kofar dake gefen falon, sai ga ni a wata karamar haraba, kusa da gen hannu nasa na dauka da bokitin na nufi fomfon dake kallon kofar na kauna na wanke bokitin sannan na fito, tsaye nai a falon inata tunani inda za samu omo na ko man wanki na zuba a ciki. Ganin bata fito ba yasa na bar ruwan a nan na koma da Tsintsinyar bedroom dinta na share shi tsaf na kwashe na na fito da datti sai kuma na rasa inda zan zuba, gashi ba ta fito ba balle na tambayeta, a dole na aje ta jikin kofa na koma dayan bedroom na share na gyara komai sannan na sauko kasa na share falon har karkashin kujera na shiga kitchen na share na hada kayan wanke wanke guri daya, a kusa da tab na samu omo sai naje na zuba a cikin ruwan mopping din na koma dakin na mopping sannan na shiga bandakin na wanke na dawo falon nai mopping na goge ko'ina sai kuma na koma kitchen din na wanke kayan cin abincin bayan na gama nai mopping din kitchen din sannan na fito na zauna a falo ina kare masa kallo a pop kadai na san ba kananan kudi aka kashe ba, balle kuma irin manyan kayan alatun kawata falo da aka cika falon da su. Ko agogon falon irin wanda na ke gani a tv ne. ALIYU POV. Yana shiga dakin Rahma ta biyo shi tana fadar ita bata yarda da wannan yarinyar ba shi ru yai be ce mata komai ba, yai kamar be ji ta ba sai latsar wayarsa yake. “Ka ji, ni fa ban yarda da ita ba, jiya ta shafa wani a fuska ta zo nan duk baki yanzu kuma ya saka nikab” Sai a lokacin ya dago ya kalleta. Kamar zai yi magana sai kuma yai shiru ya sake mai da hankalinsa gurin wayar. “Kana jina fa” “Mi kike son? Ke kika damu a samu mai aiki ai” Ya fada ba tare ya kalleta ba, sai tai fushi tana mikewa tsaye yai saurin riko hannunta ya dawo da ita kusa da shi ta zauna. “Kin cika son saka bacin rai a zuciyarki Dear, kuma kin san matsalarki, idan mai aikin ce ba ki so ai sai ki koreta kawai” “8k din da ka bata fa?” Yai murmushin kasaita yana kallon goshinta. “Ai kyauta na bata ba dan aiki ba” “Aa gaskiya sai dai tai mana aikin one month sai mu koreta, dama dai ba ka ba ta kudin ba” Kara matsawa yai kusa da ita yasa duka hannyensa ya rike fuskarta. “Idan na ga mutum cikin rashin lafiya, ina tausaya masa sosai, saboda na san zafi da ake ji, musamman idan mutumen nan makusancin ka ne, na auna kaina a matakinta, kin tuna lokacin da muke ta yawon neman lafiyarki?” “Waya sani ita ko karya take, wata kila ma muguwa ce shiyasa take rufe fuska” Be sake ce mata komai ba ya kwantar da ita kirjina ya cigaba da latsa wayarsa. After like one hour ta ďaga daga jikinsa ta sauko downstairs ganin Ataa zaune tana kallo ya bakanta mata rai sosai domin ba kowa take son yana morewa da abunta ba. “Kin gama sharar ne da kika zauna kina kallo” Ataa ta juyo da sauri jikinta har ba ri yake ta kalleta. “Eh na gama tun dazu na share ko'ina na gyara” “To daga yau karki sake rufe mana fuskarki, idan ba za ki iya bude fuska ba ko zauna a gidanku ba yadda za ki zo ki cutar da mu ki tafi ba tare da mun ha fuskarki ba” “Wallahi ni ba na cutarta kowa” “Ai ba za a iya ganewa a fatar ba ki ba, shiga dayan dakin ki wanke bathroom din kuma ki gyada dakin” Tana fada mata sannan na nufi kitchen dinta dan tabbatar idan kayan sun wanku. ATAA POV. Daukar tsinsiyar nai na hau sama a doshi dayan dakin wanda na ke saka ran shine dakin mijin, ciki tsoro da fargaba nai knocked, sannan na ja baya kadan na tsaya ina ta jiran ace min na shigo amman shiru, sai hakan yasa ni jin babu dadi, daga fara aikina a yau na fahimci daga matar har mijin kamar ba su san darajar dan adam ba, wata kila kuma saboda na kawo kaina ne, ni da kaina ina nema shiyasa suke wulakanta ni oho. Na fi karfin minti talatin a tsaye bakin kofar sannan ya fito yana ta kamshin turare, har wani matsawa yake kai ya ra6o ta kusa da ni ya sauka downstairs.   Be ba ni izinin shiga ba, dan haka ba zan shiga na taba wani abun da zai iya zan min matsala ba. Haka nai tsaye a gurin na kasa sauko kuma na kasa sai duk na ji na tsawwala, wani kankanci da bakincikin suka kwankwaso min kofa, na tabbatar da a ce yar wani ce ni da ba za su bar ni a gurin tsaye ba, za su nuna min kyama ba. Suna min duka wannan saboda ina talaka kuma na raba jikinsu ina neman taimako. Da gaji da tsayuwar ne na sauko kasa cike da fargabar abunda za ta ce min da Kuma irin kallon da mijinta zai min. Tana zaune kan kujera ita kadai tana waya, da alama wayar tai mata dadi sai kyalkyalar dariya take tana buga kafa kasa, ni dai kallonta kawai na ke, irin rayuwar jindadi da take ciki ta burgeni ga ta cikin farinciki abunda na ke ta marmarin samu amman ya gagara, zaunawa nai kasa tile har ta gama wayar sannan na ce “Be ce min ya na shiga ba, ni kuma ban shiga ba, gudun kar na shiga ya zama laifi” “Ya ce baya son ki gyara masa dakinsa” “Yanzu zan iya zuwa gida kenan?” “Idan kin ga dama” “Na gode” Sai na nufi inda na dauko tsintsiyar na maida, sannan na dawo na dauki dattin sharar na fita da ita daga gidan gaba daya, can karshen layin unguwar n samu wata bola na zuba ta a ciki sannan na dawo na aje shi a inda na dauke shi na yi mata sallama ban jira ta amsa ba, na kama hanyar gata zuciyata na mugun kuna kamar an dora ta ka ce garwashin wuta.   Ina tafe ina ta tunanin kamar ba zan iya jure aiki a gidan ba har na tsawon wata daya, saboda yadda na fahimcin hayyarsu da dabi'unsu ba kamar na kowa ba ne, sai dai idan ban yi aikin ba kudin su fa? Ai dole na biyasu bayan kuma na riga na taba wani abu daga ciki kuma ina da bukatar kudin.   Kamar yadda aka kai ni dazu haka wani mai achaba ya dawo da ni na bashi naira hansi sannan na shiga gidan, ina yin sallama Farida ta amsa tana wanke wanke, fuskarta da far'a kamar kullum ni ma na yi kokari aron murmushi na yaba a fuskata duk kuwa da kasancewar shi a kusa da ni. “Har kin dawo? Nana tace min kin samu aiki?” “Eh na samu, yau na fara” “Allah ya taimaka, wane unguwa?” “Nasarawa” Na bata amsa ina shiga inda Nana take, wanann karon a zaune na same ta ta saka dayan hannunta ta dafe gefen cikinta tana hawaye. Da alama ciwon ne ya taso mata domin ba abu kadan ke kasa nana yin hawaye ba musamman ciwo. Kusa da ita na zauna na rafka uban tagumi ina ta kallon saukar hawayenta, ban san abunda zan yi ta samu lafiya ba, ban zan zwa zan kaiwa kuka ya saurareni ba, Doc Asim ya zalince mu zalince mai tsanani kuma na kai kararsa aka kasa kwatar min hakkina suka kasa bani gaskiya saboda ina talaka shi kuma yana mai arziki. Sai wani numfashi take wahalce ni kuma na kasa ko motsawa daga inda na ke zaune balle nai nata sannu yadda take hawaye haka ni ma na ke hawayen, kashi ya hade min goma da shirin can ba dadi nan ma ba dadi. “Ni kadai na san irin zabar da na ke sha a kan ciwon nan, ni kadai na san yadda zafin ciwon nan yake min, ni kam da ma na mutu wata kila da na fu samu sauki fiye da haka” Cikin murya kuka ta fadi haka da sauki kasa-kasa. Hannu nasa na share hawaye na daga inda na hango kudin da na bata dazun na dauka na fito jiki ba kwari na je bakin titi gurin wata pharmacy, na fada masa yadda ciwon yake sai ya ba ni magani kusan dubu uku da dari bakwai na dawo jiki na rawa na balla na bata na shafawan kuma na shafa mata, sai na koma ta bayanta na rumgumeta na fashe da kuka marar sauti, ji na ke kamar ace ina wata dama zan iya nema mata lafiya ta warke ita kadai ta rage min idan ta tafi ta barni ban san halin da zan shiga ba. Na dade rumgume da mahaifiyata sannan na saketa ta kwanta, ni kuma na goge fuskata na fito tsakar gidan ko za a samu sassaucin abinda na ke ji a zuciyata. Da na fito sai Farida ta dasa min wata sabuwar fira dama akwai da yawan magana, a nan take labarta min cewar mahaifinta ne ya ce Nana ta dawo nan ta raba ta zauna tun da mai wacan kangon gidan ya koreta gashi bata da wani gurin zama. Ni kaina nasan indai Farida ba to ko sai mahaifinta, domin mahaifiyarta ba zata taba yarda tace ta zauna a gidan ba. Bayan sallah magariba na dauki kudi da kwano na siyawa nana tuwon masara da miyar yauki domin shine mai yar nasiha ba kamar shimkafa ba mai tsada, ko da na shigo na tarar ta samu sauki sosai tana zaune saman dankwalinta da tai sallah. Gaba na saka ta na cilasta mata cin tuwon ita kuma ta ki ta ci ala dole sai ni na fara ci, a dole sai na ci sannan ita ma ta ci na kawa mata ruwa ta sha, sannan muka gabatarda Allah isha'i muka kwanta a gurin da mutum ba zai iya mike kafafuwansa ba straight ba.    ***      ***      *** Da wuri na farka gudun kar nai lattin zuwa gurin aiki, bayan na ayi alwala ita kuma na samo mata kasa tai taimama ta yi sallah asuba, cikin kudin na dauka naje na siyo mana koko da kosai da suga na kawo muka karya sannan na shiga bandaki nai wanka da ruwan sanyi duk da kasancewar akwai sanyin safiya da be gama sauka ba.   Bayan na fito na saka wasu tufafi, daman can shafa mai be dame ni ba bayan cikin tsarina wankan ma gudun kar suce ina wari da ba zan yi ba. Haka na shirya cikin wata kodaddiyar atamfata na sake kwaba gawayi kamar ranar na shafa a fuskata, tun da sun ce na daina saka nikab sai na saka bakin gawayin da na saba sakawa duk kuwa da irin kazantar da suke ganina da shi.    Yau ma sai da na dauki naira dari a cikin kudin sannan na saka Hijab dina na yi ma Nana sallama na fito na shiga dakin Maman su Farida na gaishe ta ita da mijinta shi ya amsa da far'a sabanin ita da ko kallon kirki bata min ba, wata kila tana ganin kamar mun takura tane mun zauna mata a gida mun hana ta wali a yadda a gidanta. Yau ma achaba na hau na fada masa inda zai kai ni, ba aje ni ko'ina ba sai bakin gate din gidan na mika masa kudinsa na sauka, ina kokarin yin knocked gate din sai na ga an bude shi gaba daya, ashe mai gidan ne zai fita sa na raba gefe sai da ya fice sannan na shiga ina mikawa mai gadin gaisuwa bayan ya amsa min na nufi kofar gidan wato kofar babban falon da zai sada ka da cikin gidan gaba daya. Da nai knocked din kofar sai na zauna kusa da kofar dan nasan ba yanzu zata bude min ba, haka nai ta zama a gurin har mai gidan ya dawo ya faka motarsa inda sauran motocin suke ya fito fuskarsa da Annuri da haifa ya nufo kofar ya saka keys din hannunsa ya bude. “Ina kwana?” Be amsa min ba, sai kallon fuskata yake ta yi wata kila yana mamakin yadda yau ban saka nikab dinba na sake shafa bakin gawayi, ni dai ban kalleshi ba domin matarsa ta fada min mijinta baya son kallo. Shi ya fara shiga sannan na bi bayansa na shiga kai tsaye na nufi gurin jiya na dauko tsintsiyar da mopper na fara gyara falon sannan na shiga kitchen na gyara, ban san a wane dakin ta ke kwance bana son na shiga ta ce na mata ba dai-dai. Sai kawai na nemi gefen kujera na zauna, ina ta jiran fitowarta shiru har bachi ya dauke ni a gurin ban sani ba. Can cikin bachin nawa na ji an watso min ruwa mai dumi hakan yasa ni farkawa a firgice, ashe ruwan tea da ke hannunta ta watsa min. “Ina kwana” Na mika mata gaisuwa kamar a rikice. “Ba ki yi bachi a can gidanku ba ne da za ki zo nan kina mana bachi? Ba aiki aka dauke ki ba?” “Na gyara nan na gyara kitchen ina jiran ki fito sai na gyada dakunan” “Miye a fuskarki kuma?” Na yi shiru ban ce mata komai ba sai kawai ta tabe baki ta zauna a kan kujerar. “Shiga ki gyara min bedrooms dina” “To” Na amsa a ladafce sannan na dauki tsitsiyar na nufi dakunan na gyara na na dawo na dauki mopping na goge ko'ina na wanke bandakunan sannan na sauko. “Na kare” Na fada mata bayan na maida kayan inda na daukosu. A gurin ta bar ni tsaye bata ce na tafi ba, ba ta ce na tsaya ba, har jikinta sauko hannunsa rike da agogon hannu yana kokarin sakawa. “Kin tabbatar za ki iya driving da kanki? Idan ba za ki iya ba don't stress yourself zan turo direba ya kai ki” Shine abunda ya fada mata, ita kuma ta girgiza masa kai. “Aa zan iya, wannan yarinyar za ta rika min kayan” A gabana ya kai bakinsa a goshinta ya sumbace ta babu ko kunya, shi da kiss ni da jin kunya har na ji kamar kasa ta nutse da ni da kunya. Be yi minti talatin da fita ba ta hau sama ta bar a gurin a tsaye ina ta jiran saukowarta, sai da tai wanka ta shirya cikin wani lace mai kyau da tsada sannan ta sauko idonta sanye da katon bakin gilashi nan na mata. “Shiga dakina ki dauko min ledodi ki saka mota” Abun ka da mai jiran umarni sai nai hanzari cira kafa na taka har dakin na dauko na kai gurin motar da ta bude na zuba su a baya, sai kuma nai tsaye ina jiran abunda za ta ce min. Bayan boot din taje ta dauko wani tawul ta miko min. “Shimfida wannan a baya sannan ki zauna karki shafa min dattin jikinki a mota” Na saka hannu na karba cike da jin zafin furucinta, na shimfida kamar yadda ta fada sannan na zauna ita kuma ta shiga mazaunin direba tai ma motar keys, muka fita ba tare ni na san inda za mu je ba, nawa ido ne kawai ina ta kallon titi har muka isa wata kyakkyawar unguwa mai manyan gidaje, gida hudu muka wuce sannan ta danna horn mai gadin ya bude mata gate, a inda sauran motocin suke ta faka motarta ta fito sannan tace da ni na fito ya dauko mata ledodin, tana gaba ina bayanta har muka shiga cikin gidan. Alhajin nan mai kangon gidan da ya kore mu na hango zaune kan kujera yana dariya an zagaye shi suna ta hayaniya da alama wata wainar ake toyawa. “Daddy... Happy birthday” Hajiyar ta fada tana nufar inda yake, ban yi mamakin wulakancinta ba indai har wacan mutumen marar ganin tausayi ne mahaifinta *Z A K I* By Khadeeja Candy 1️⃣3️⃣ A gidan ta wuni ita da mahaifinta da sauran yan'uwanta suna ta tayashi murnar birthday kowa na kalla fuskarsa dauke da farinciki,kamar wadanda aka yayewa damuwa har abada. Sai da yamma mahaifinta ya fita ya barsu a cikin gidan suna ta shagalinsu. Duk iya shagalin da akai da ciye ciye da akai Ataa na waje zaune ita kada kamar yadda Rahma ta umarce da zama waje, sai misalin sha daya na dare ta fito cikin gidan baya ta yi waya da Aliyu ta fada masa ba zata iya driving ba ya zo ya dauke ta.   Ko da ta fito Rahma na kwance a balcony, matsawa tai ya saka fada ta dan musgune ta kadan ita kuma ta farka a girgice sannan sai ta jefa mata dari biyu “Tashi ki je gidanku” “To” Ta fada tare da saka hannun ta dauki kudin ta gyara Hijab dinta ta kama hanya. A gurin Rahma tai tsaye har Aliyu ya iso da motarsa harabar gidan ya faka. Sannan na soma takawa a hankali ta karaso inda yake, fito yai daga cikin motar ya bude mata front seat ta shiga ta zauna ya rufe ya koma cikin motar yai nata key ya danna horn aka bude musu gate. Lokacin daya hau titi ya fara tafiya sai ta kwanto jikinsa, shi kuma ya kai hannunsa yana taba kanta da yake ji da zafi. “Kina jin rashin lafiya ne?” “Eh” “Since when?” Ya faka motarsa gafen titi ya juyo yan fuskantar da kyau. “Dear miyasa kike wasa da lafiyarki ne? Ba ki san lafiyar ki tana da amfani a gurina ba? Tun yaushe kika so ma jin zazzabi” “Da yamma nan, yanzu ne ya fi min sosai” Wayarsa ya ciro ya kira Doc Asim bugu biyu ya dauka. “Doc same ni gida yanzu, jikin Rahma ya tashi” Yana fadar hakan ya kashe wayar ya jana motar @360 suka iso gida, ba su yi minti ashirin da isa ba sai ga Doc Asim ya iso, tana zaunen falon kusa da Aliyu ya tambayeta abunda ta ke ji ta fada masa ya bata magani, sannan Aliyu ya rika ta suka shiga bedroom ya kwantar da ita, bakin gadon ya zauna kusa da ita yana ta kallonta kamar mai auna hawa da saukar numfashinta, har bachi yai gaba da ita, sannan na taso ya fito daga dakin shi ma saboda kiran wayar da Mama Fulani tai masa ne, saukowa yai kasa yana amsa wayar. Yadda fuskarsa take sake duk kuwa da irin tashin hankalin da ke ransa na ciwon matarsa, amman ka ga murmushi a fuskarsa ka san mai kiran yana da muhimmanci gare shi. “Aliyu ka yafe kowa ka kyale mu ko?” “Na isa Mama? Ai ko zan yafe kowa ban da uwata matukar ina neman albarka” “To ya gida ya matar ta ka?” “Gida kalau surukarki kuma tana nan yau jikin ya soma tashi” “Subhanallahi fatar dai da sauki” “Da sauki ta samu bachi ma” “Masha-Allah Allah kara lafiya, zan je Dubai gobe, ba lallai idan na je can na kira ka ba, fada min abunda kake son na siyo maka da matarka” “Ni dai perfume na ke so, ita kuma ki siyo mata duk abunda kika ga ya dace” “To shikenan, a gaishe ta idan ta tashi” “Zata ji thank you Mama” “Allah maka albarka” Daga haka tai hanging. Shi kuma ya tashi cikin rashin kuzari ya nufi kitchen, tea ya hadawa kansa ya dawo saman kujera ya zauna ya kunna tv for like ten minutes ya tashi ya koma dakin matarsa. ATAA POV. ban taba auna rashin imani da tausayin irin na matar nan sai yau, ta ba a gidan zan kwana ba amman ta kyale ni na zauna a waje bata ba ni abinci ba na wuni da yunwa ta bar ni a haka, yanzu kuma sha dayan dare ta ce na kama hanyar gidan, gashi ko abun hawa babu, tsoro da fargabar abunda zai same ni, wa zai tare ji a hanya barayi ko masu cin zarafin mata duk be dame ta ba, saboda kawai ina nema a karkashinta, shi kenan dan ina talaka ba ni da gata, ni fa ya ce kamar kowa ba daga sama na fado ba, amman saboda ba ni da shi ina talaka a yau an sake ni karfe goma sha dayan dare na kama hanyar gida. Ban samu a abun hawa ba, a kafa nai ta takawa ina ta addu'ar Allah ya kai ni gida lafiya. Ko da na isa unguwar babu mutane sosai domin daya saura na dare. A bakin kofar gidan na tsaya nai buga kofar ba a dade ba aka bude min, babu wuta a lokacin dan haka mahaifin Farida ya haske min fuska da fitila. “Ataa ke ce cikin daren nan? Ina kike je?” “Gurin aikin ne, muka fita ba mu dawo ba, sai yanzu” “Ina kuka je?” “Gidan iyayenta” Sai ya bude min kofar na shigo yana ta kallona kamar be yarda da ni ba, sai da na shigo cikin gidan na hango Nana tsaye rike da bango tana kallona lokacin da na karasa kusa da ita sai na rasa me zan ce mata, na sani dole hankalinta ya tashi rashin ganin na dawo, gashi babu mai mata wata hidimar sai ni. Rikata nai muka koma cikin dakin sai da ta fara zama sannan na zauna kusa da ita na fada mata dalilin dadewar da nai ban dawo ba. “Da wani abun ya same ki a hanya fa?” “Nana matar nan da na ke yi ma aikin yar mai kangon gidancan ne wanda ya kore mu, ina ganin gaba daya danginsu basa da mutumci ko kadan” Na fada cikin muryar da ke Nun a gajiye na ke ga kuma yunwa da na ke ji rabon da na saka wani abu a cikina tun karin safe da na sha koko da kosai. Sama-sama mu kai fira da Nana ta nuna min rashin jindadinta na dadewar da nai a can sannan muka kwanta ni da ita.    Yau ma kamar jiya na tashi da wuri saboda matar nan ta fada min na rika zuwa tun karfe bakwai na safe, na san idan na tsaba lokaci wani abu zai iya biyo baya, waina na siyowa Nana ta karya sannan na fito na wanke kwanon da ta ci na maida na janyo ruwan rijiya na yi wanka na saka doguwar rigata ta atamfata kodaddiya, ban damu da saka dankwali ba, na fita waje na daddaka bakin gawayin na shafa a fuskata, na saka Hijab dina na fito na leda dakin Maman su Farida na gaisheta sannan na saki labulen dakin har na kama hanyar fita sai ga Farida ta fito sanye da uniform din makaranta tana cewa na tsaya mata. “Har kin shirya zuwa aikin tun da safe haka?” “Wallahi matar da na ke aiki gidan ta ne bata da mutunci ko kadan, tace na rika zuwa bakwai kin ga idan na tsaba zata iya korata gaba daya” “Gaskiya kan bata da mutunci, tun da har zata rike ki ki kai karfe daya na dare sannan ki dawo, ni wallahi da za ki biye ni da kin yarda maman Salma ta sama miki aiki a Abuja, acan take samawa mutane kuma Wallahi albashi mai tsoka” “Kai anya Farida zan iya zuwa har Abuja? Kin ga Nana ai bata da wanda zai kula da ita sai ni” “Amman ai dan neman lafiyarta da abincin ta za ki yi, kuma idan ya wadace ku ya kamata ki dauke ta kuje har garinku ki nemi danginku, zama a nan babu kowa a tare da ku ba zai amfana muku komai ba” “Nima ina tunanin haka, amman na fi son sai Nana ta samu lafiya tukuna” “Allah ya bata lafiya, nawa ne suka dauke ki aikin?” “8k ne” “8k mi zai miki? Ai wannan kudin zai iya karewa a abinci kawai, gaskiya kara ma Abuja nan ance can fa irin manyan gidajen nan har 30k 50k ana bawa mutum, kin ga da kin hada na wata uku ai ya isashe ki” “Da gaske Farida” Na tambaya cike da kwadayin tabbatar da zancen nata. “Wallahi haka Maman Salma ta ce min” “Ai ba zuwan ba, kin ga dama ace Lukman yana da rai dazan samu sauki wanda zai kula min da Nana amman yanzu bata da kowa ai sai ni, ita kanta ba zata yarda na tafi ba” “Gaskiya haka ne, amman indai ina nan ni kaina ai zan iya kula da Nana kin sani, ko da ba zan cire mata kewarki ba zan rage mata shi, ko ba zuwa aiki ba ai dole wata rana za ki yi aure ki tafi ki barta, ko da yaki kin ki bari ma aga fuskar na ki kullum sai boyo kike” Na yi murmushi ina kallonta a yayinda muka kawo a hanyar da za mu rabu. “Farida kenan, ni ban taba kawo wa kaina tunanin aure ba, ban taba lissafa kaina a cikin matan da za a iya aure ba” “Saboda?” Ta tambaya cike da mamaki. Sai na sake yin murmushi a karo na biyu na ce. “Ba ni wannan lokacin da zan tsaya na yi fira da wani namiji ba, kullum tunanina ina abinci zai shigo, yanzu kuma tunani ina kudi za su shigo na nemawa Nana lafiya, bayan haka maza basa son yarinyar da bata da arziki a gidansu, sun fi son aure yar masu kudi ko mai rufin asibiti, amman irina idan aka ce za amin aure na san daga ni sai tabarma za a kaini, wanda na san hakan zai iya janyo min wulakanci da kankanci a gurin mijin da yan'uwansa” Kallon hawayen da suka cika idona ta tsaya yi sai ta rumgume itama idonta cike da kwalla. “Za ki yi aure kawata, In-Sha-Allah za ki auri mutumen da zai dauki dawainiyarki har da ta Nana ma, na saka ki gaban mota yai ta yawo da ke a garin nan” Na sake ta ina yar dariyar zancenta. “Farida kenan, wa zai yi mace irina haka? Mace da batai boko ba, bata waye ba, bata iya komai ba sai bara da roko a titi? Babu wanda zai so auren makaskanciya” “Ataa karki yanke kauna daga rahamar Allah, dan jarrabe ki a haka ba shi yake nufin ba za ki samu jindadi a gaba ba” “Na sani, kawai ina duba yanayin rayuwar ne, duniyar ta canja ba kamar da ba ne, ke dai ki tafi makaranta kar ki yi latti” Daga haka muka rabu ita ta wuce makaranta ni kuma na kama hanyar zuwa gurin aikina, ina ta kwadayin zuwa makaranta amman ba hali, lallai karatu da samun wanda zai tsaya maka ka yi karatun gata ne. Ina tafe ina ta sake sake na har na isa, yau kan ni kaina na san na yi rana zuwa domin a kafa na zo kamar yadda a jiya din ma na dawo a kafa duk kuwa da irin tazarar da ke tsakanin unguwar mu da ta su. Sai da nai knocked gate din sau biyu sannan aka saka bude min gate din na gaishe shi kamar yadda na yi jiya sannan doshi cikin gidan, na yi mamakin tararda kofar falon abude wata kila wani dalilin ne ya saka suka bude kofar. Ni dai na shiga da sallamata duk da nasan ba za a amsa min ba, haka kuwa akai domin mai gidan nan na hakince saman cushion amman be amsa min ba duk da idonsa na kaina har na karasa tsakiyar falon na gaishe shi nan ma be ce min komai ba. Ban damuwa ba, domin a tsakanin jiya da shekaranjiya kawai na fara sabawa da halinsa da dabi'unsa, matarsa ta fda min baya son yawan kallo, sai dai na lura shi din yana da kure mutum da ido har ka soma tsarguwa sai kuma ace wai kai ba zaka kalleshi ba, lallai masu kudin nan akwai su da rashin adalci da takura rayuwa. Abu na biyu na lura baya son yawan magana kuma yana da kyama sosai fiye da matarsa, ga kamshi a duk inda ya wulga ko ya zauna, kamshin turarensa ne ke yiwa mutum sallama tun gabanin shi yai maka, akwai kwarjini sosai idan kana kallonsa, haibarsa tana fitarta da siffar zatinsa da ainahin kyauwunsa, ban taba ganin murmushinsa ba, a tunani murmushi kamar ba zai yi ma fuskarsa kyau ba, duk kuwa da kasancewar yana cikin sunnar Manzo na, sai dai nana jin wannan miskilin ya ta6a ďa66aka sunnarsa ta murmushi balle kuma har ta kai shi ga yin dariya. Gurin da na dauki tsitsiya jiya na nufa na dauka tare da mopper na nufi kitchen, can na ke ra'ayin na fara gyarawa tun da na ga shi yana zaune a falon, waya sani ita ko bata tashi bachi ba, balle na gyara bedrooms. Ina cikin aikina na ji tsayarwar mota a harabar gidan, sannan na ji sallama da muryar da na ke kyautata zaton kamar na san mai ita, sai da na gyara kitchen din tsaf sannan na riko tsintsinyar ya fito daga kitchen da zimmar gyara dinning area da falon idan magajin izzar ya tashi. Arba idanuwa sukai da mummuna mutum wanda zan iya kiransa da bakar jaddara, da bana son na sake saka ta a idona har a bada, Doc Asim ne sanye da suit ya dora labcoat sama yana zaune akan kujerar da ke fuskantar wacce Rahma take zaune ita da mijinta... _____________________ Page biyu ya rage mana mu gama free pages In-Sha-Allah. if you want to subscribe pay 300 to 0314795884 Abubakar Hadiza Gt Bank. sai ku turo shaidar biyan wato screenshot ta wannan number 08036126660, ko kuma katin mtn na 300 ga marasa account ta wannan number 08036126660. yan nijar za ku tura 500fc na line Orange ko Airtel ta number nan +22790165991 sai ku min magana ta wannan number 08036126660 Za'a saka ku Group. Thanks 🙏🏻 Ku ziyarci YouTube channel dina, ku danna min subscribe kuma kui sharing. 👉https://www.youtube.com/channel/UCpAkml0pIh6MUnzt9nLh_qQ *Z A K I* By Khadeeja Candy 1️⃣4️⃣ Bana bukatar na tambaye abunda ya kawo shi gidan, kasancewarsa likita, da kuma yanayin da naga Rahma na tabbatar bata jindadi, sai dai ina tabbacin ba su san ko waye Doc Asim ba, shiyasa har suka kira shi har cikin gidansu, akwai yiyiwar ya sake samun damar sake cutarsu kamar yadda ya cutar da ni. Kallonsa kawai da na ke ina jin kamar naje na shakeshi ya mutu. “Ke lafiya kika tsaya kallon mutane ba za kije ki yi aikin ba?” Rahma ta daka tsawar data saka ni dawowa hayyacina. Sai mijinta yai saurin rike hannunta yana alama da tai shiru kar ta wahalar da kanta gurin magana. “Karku yarda da wannan mutumen Wallahi azzalumi ne macuci, mugu wanda ba zai taba gamawa lafiya ba” Da sauri Doc Asim ya dago yana kallon inda nake tsaye da mugun mamaki, da alama sai yanzu ya san da tsayen da nai jikin kofar. “Wacece wannan?” Ya tambaya yana kallon Mai gidan da ke kallona shi da matarsa. “Ba ka gane ni ba?” Na fada kana na saki tsintsiyar hannuna na juya na koma kitchen din na cire Hijabina abun ka da marar dankwali sai gashi na sauko har gadon bayana, na zuba omon da ke gurin na wanke bakin fuskata na juyo na fito a fusace na karasa har kusa da inda yake zauna na nuna masa fuskata. “Ka ganene yanzu? Bayan ni wace yarinyar ka cuta? Bayan ni wace macen ka sani mai kama da ni?” Miyewa yai tsaye ya wanke min fuska da mari. “Ba ki da hankali ke kin taba ganina ne?” Tasss na mayar masa da martanin marin da yai min cikin zafin rai, duk da kasancewar ya girme ni a shekaru da jiki. “Na mare ka da hujja sai ka samu damar sake saka yan sanda su kulle ni a cell kamar yadda ka sa aka min saboda ina talaka” Yadda muryata take fita kadai ta isa ta karantar da kowa irin daci da dafin bakincikin da ke raina, ga wasu zafafan hawaye da suke sauko min, ina yi ma Doc Asim wani irin kallo mai guba. Mamaki ya hana shi motsi sai sakin baki da yai yana kallona, Rahma ce ta mike tsaye. “Ke ashe baki da hankali ba ki da tarbiya? Za ki daga hannu ki mari babban mutum mai daraja kamar Doc Asim? Kina yar talaka?” “Ba yin kaina ba ne talaucin, ke ma da Allah ya zabi a gidan masu arziki ba yin kanki ba ne, ba wata gwaninta kikai wa Allah ba ya zabe ki ya bar ni, saboda kawai ina talaka ba shi yake nufin ni ba mutum ba ce, a gurin ki Doc Asim yake mai daraja amman a gurina konanniyar ashanar bola ta fi shi, zan fi jindadin sunan mutuwa fiye da sunan wannan azzalumin, ganin bakin duhun zai fi min ganin wannan mutumen” Na fada ina nuna shi da yatsana, mamaki ya cika Rahma, mijinta kuwa kallona kawai yake sai kuma ya kalli Doc Asim kamar mai son tantance abu. Doc Asim ya jinjina kai yana kallona yai kwafa. “Ni kika mara? Sai kin yabawa aya zakinta, ni ban sanki ba ban san inda kika fito ba amman sai na nuna miki ko wanene ni” “Babu abunda zaka nuna wanda ban san shi ba, na sanka na san zalincika tun har ka iya cire kodar mahaifiyata ba tare da saninta ba, saboda kawai ka maida ni zahila marar galihu, ka sa na saka hannu kai mata aiki ka cire mata koda, kuma kasa aka kulleni a gidan yan sanda saboda na nemi hakkin mahaifiyata, to wane zalinci zaka nuna min da ya wuce wannan? Idan kashe ni kaka son yi, to mutum baya mutuwa biyu, domin ni na dade da mutuwa tun daga lokacin da kasa mahaifiyata ta rasa lafiyarta, sanadin haka na rasa kanena, to me zaka min yanzu? Duk abunda kake jin zaka iya yi kaje kai, ba a duniya za a tabbata ba, akwai kiyamar Allah zata tsaya, kuma ni da kai za ku amsa ko wace tambaya daga Ubangiji...” Na karasa ina fashewa da kuka tare da juyawa da zimmar zuwa na dauki tsintsiyar na cigaba da aikina, sai naji muryar mijin matar nan yana wata irin magana mai rikitarwa. “Kardar kodar da aka dasawa Rahma take magana....?” Juyowa nai idona na hawaye na nuna Rahma. “Kodar Nana ka sakawa wannan matar? Matar da mahaifinta ya koremu a kangon gidansa saboda mun taba a gidan? Matar da mahaifinta be san daraja talaka ba? Matar da mahaifinta yasa a ka wulakanta mu? Ita ka sakawa kodar talaka? Talakar ma wacce ya wulakanta? Ka cuce ni ka cuci nana Allah ya isa tsakanina da kai, da kai da duk wanda yasa kuka aikata min wannan aikin ba za ku ga da kyau ba, Wallahi Allah ba zai barku ba” Na fada cikin daga murya iya kar karfina, sam na manta da a gidan wani mai kudi nake, yau duk wani tsoro da fargabar gudun laifi ya fita a raina, daga Rahma har mijinta da Doc Asim yau kananan mutane na ke kallonsu kuma azzalumai. “Uban waye yace ki siyar? Akan mi za ki rika fada mana magana son ranki cikin gida? Ubana sa'arki ne da zaki rika saka ko a maganar ki?” Rahma ce ke wannan maganar tana matsowa kusa da ni, har ta ka hannu zata mare ni sai mijinta yai saurin rike duka hannayenta ya matsar da ita jikinsa yadda ba zata iya ko da kwakwaran motsi ba. “Talauci ba hauka ba ne Rahma, kuma ba kaskanci ba ne, jarabawa ce daga Ubangiji, ba kuma zan sake yarda marar sanin darajar dan adam irinki wacce ta more da kodar mahaifiyata ta sake wulakanta ni ba, kin ci riba da ni tun da nayi aikin kwana biyu a karkashin ki, amman ba za a koma ba, ya zama na karshe, sai dai ki wulakanta wata amman ba ni ba, kuma tun da har kuka zalinmu lafiyar nan da bata yi amfani komai a jikinki ba” Ina kawai nan na nufi kitchen din a fusacw na dauki Hijab dina na saka na fito fuuuu na fice daga gidan kamar iska. Kan kace kwabo har na kai gate na bude na fita raina na min mugun zafi zuciyata na ciwo sosai. A rayuwata ban taba ganin mutane masu son kai da tsantsan zalinci kamar likitan nan da mutanen nan ba, babban bakincikina sun ci riba da ni na aikin da nai a karkashinsu, wanda hakan ya fi komai yi min ciwo. Tun da na kama hanyar gida sai na nemi kukan zuciyata da na ido na rasa, wani karsashin da karfin zuciya dana ruhi suka rufe ni, na jaddawa kaina nemawa Nana lafiyata ta rayu ko dan bakincikin masu son ganin bayanta, a yau na gane ba kuka na ke bukata a yanzu ba, lokacin kuka da bakincikin abunda ya faru a baya ya kare, wannan lokacin na fuskartar gaba ne da inganta rayuwata da ta Nana, na yarda abunda ya tafi baya dawowa amman abunda be zai zo za a iya tarbarsa gabannin ya zo, zan jure ko wane kalar wulakanci da cin zafi daga duk wanda zai iya zama dalilin samun lafiyar Nana. A kullum idan zanje gida ina zuwa da kasala da jin gajiyar tafiyar, amman a yau na isa gida da karfi kamar daman can ban yi tafiyar ba, ban yarda Nana ta fahimci komai ba, na shiga dakinta na zauna ina ta kokarin yin far'ar da take ta zo min. “Lafiya kika dawo da wuri haka Ataa?” “Nana sun koreni daga aikin” “Innalillahi wa'inna ilaihirraji'u, sun kore ki kuma? Me kikai? Mun shiga uku” “Ba mu shiga uku ba, kuma da yardar Allah ba za mu sake shiga uku ba, ina tunanin ma kamar wata hanyar zata sake bude mana?” “Kamar ya? Yanzu ina za ki sake samun wani aikin” “Farida ta fada min cewar Maman Samawa tana samawa mutane aiki a abuja, kuma a can ana biyan kusan 30k ko sama da haka, kin ga cikin wata biyu ko uku na hada kudin maganinki” “Aa ni ba zan yarda kije can nesa ba, ban san iya abunda zai iya samunki ba, kuma nan wa zai kula da ni idan ki ka tafi?” “Farida ta min alkwarin kula da ke, idan har za ki iya hakurin ciwon nan na ki zauna asibiti na tsawon wata biyu, zaki iya hankurin rashin ganina na wata daya, idan na samu lokaci sai na zo na ganki ni dai amincewar ki na ke bukataka kamin nai ma maman salma magana, ina son lafiyarki Nana, sai da lafiyarki zan iya neman dangina, hankalina kuma ya kwanta, dan Allah ki amince Nana” Na fada ina kama hannayensa sai naga yanayinta da fuskarta sun canja. “Ko daga nan zuwa wani gurin za ki je, ina jin tsoro Ataa sai naga kamar ba za ki dawo ba, bana son ki zo yi ta wahala da gawa waya sani ko ba zan kai wani lokacin ba” “Da ba zaki kai wani lokacin ba, da baki rayuwa bayan wannan lokacin da akai miki tiyata ba, kuma babu wanda yasan rayuwa da mutuwar wani sai Allah, kina karya min guiya, ki rika nuna min cewar zamu rayu ni da ke ko da mu kai muka rage a duniya, dan Allah Nana ki barni nai wannan jihadin, ki bar ni na samun wannan faricikin da ladar” Magangannun nai ta mata ina lurar da ita har na samu ta aminta duk da kasancewar ba ta so haka ba. Bayan sallah azahar na ja Farida muka kama hanyar gidan maman salma da shiga mu kai sallama muka gaisheta, sannan Farida ta koro mata da bayanin da ke tafe da mu, wani abun mamaki da jindadi sai tai murna da hakan har take labarta mana cewar daman ana neman mai aikin a wani babban gidan masu kudi da ke Abuja, sai dai tace ba zata yi komai ba har sai ta zo gurin Nana ta ji ta bakinta dan tabbatarwa, ni kuma na ce mata na yarda ta zo su yi magana, sallama muka mata muka kamo hanyar gida wani dadi ya lullube ni na soma yarda da cewar kukana ya kusa karewa... ALIYU POV. Zai iya rantsewa a rayuwarsa be taba haduwa da wata mace yar talakawa mai karfin zuciyar da ta iya tsaya gabansa ta fadawa Rahma magana son ransa ba sai yau, for the first time yau wata ta ciwa Rahma mutunci ya kasa yin komai, har yanzu fuskarta yake gani irin kyau da haiya ta yai arba da shi a fuskarta a yau ko a mafarki be ci karo da macen da kallonta ya saka shi faduwar gaba ba sai yau. Kalamanta da ďai-ďaiya suke masa yawo a kunne, kalma zalinci ita kalma ta biyu daya tsana bayan talauci, yes he's rich and he know be zama dole ya taimaki kowa da dukiyarsa ba, amman yai wa kansa alkwarin ba zai taba yarda dukiyarsa ta saka ya zalinci wani ba, ko da kuwa talakan daya kyama ne. Yasan yadda lafiyata take da muhimmanci tun daga lokacin daya fara neman ta matarsa yana jin tsoron rasa ta a ko wace dakika ita kadai da take a natsayin matarsa hakan yasa shi fahimtar Ataa wacce ita kuma take zancen mahaifiyarta. Haka sukai tsaye a falon bayan fitar Ataa har na tsawon mintuna talatin ba tare da kowa ya ce uffan ba, daga Aliyu har Rahma da Doc Asim dake ra sake saken yadda zai kare kansa. Rahma jiran take mai kare yace wani abu tun daga lokacin da Ataa ta fada mata ba daidai ba, amman bata ji yace komai ba, sai ma rike mata hannu da yai a lokacin da zata mareta. Aliyu kuma yana ta jiran abunda zai fito daga bakin Doc Asim amman ya kasa magana kamar an daure shi. “Kodar mahaifiyata ka cire aka sakawa Rahma ba tare da sanin ba?” Doc Asim yai saurin kallon Aliyu. “No karya ta ke yi? Ita ta siyar da kodar da kanta, zan iya nuna maka shaida ma, ita ta siyar da kanta” “Mi zai saka tai maka karya? You know what na yarda da komai amman ban yarda da zalinci ba, ban yarda na zalinci wani na kuma na kwanta nai bachi mai dadi ba, dan ina neman lafiyar Rahma ban ce ka zalinci wata ba, na fada maka ka nemo wacce zata saida zan biya ko dala dubu nawa ne, amman ban ce ka cire ba tare da sanin mai ita ba” “Amman Dear ai yace siyarwa tai...” “Silent” Ya fada sai dai ba cikin daga murya ba, tare da dagawa Rahma hannun wacce ke kokarin kare Doc Asim da nuna abunda yai ba dai-dai ba ne. “Ka bani amsa da saninta ka cire ko ba da saninta ba” “Ni ban san wannan yarinyar ba” Shine kawai abunda Doc Asim ya fada ya dauki akwatinsa ya fice a fusace har gumi na karyo masa idonsa su yi ja alamar ransa ya bace sosai. Yana fita Rahma ta kalli Aliyu sannan ta nufi upstairs cikin bacin rai da zazza6in da da ke kokarin rufeta. Zaunawa Aliyu yai saman cushion yana ta auna irin zalincin da akwai wa Ataa idan har ta tabbata Doc Asim ya cirewa mahaifiyarta koda ba tare da sani ba, mikewa yai tsaye ya bi bayan Rahma a bedroom dinta ya same ta zaune bakin gado tana waya be san me ta fada masa ba, kuma be san da wa take wayar ba, sai dai yana alamar kuka da hawaye a idonta, saurin fisge wayar yai ya kashe kiran sai ya kashe wayar gaba daya, ya zauna kusa da ita. “Kin sani idan kina ciwo bana son kina wani dogon motsin, za ki yi street kanki ne kawai” Kallonsa tai da duba mai mai ma'anoni da yawa idonta har ya fara ja. “Miyasa zaka yarda da yarinyar nan ka karyata likitan da ya shekara biyar yana maka hidima?” Be ce mata komai ba, ya kai hannunsa ya share mata hawayenta sannan ya rika fuskarta da hannayensa biyu yana mata magana a hankali yadda hankalinta zai kwanta. “Za mu magana daga baya, for now ina son ki kwanta ki huta, and promise me za ki yi bachi?” Ta dauke kai tana hadeye yawu. Sai ya jata zuwa kirjinsa ya rumgume, ya dan kishingida da gadon yana ta kallon sillin kamar mai tunani. Ya dauki awa daya a haka sannan ya soma jin sauka numfashinta mai zafi alamar bachi ya dauke, sai ya kwantar da kanta saman fillo ya lullube ta da blanket ya mike a hankali ya fita daga dakin dare da jan kofar dakin a hankali. Fitowa yai daga cikin gidan gaba daya, tun kan ya karasa gurin motarsa ya danna key motar ta bude, yana shiga yai nata key tun kan ya kai gate mai gadin ya bude masa gate din yana daga masa hannu, ko kula shi be yi ba ya dauki hanyar gidansu wato gurin Momy, as usual idan babu Nasir ko Mama Fulani a kusa da shi Momy ce abokiyar shawararsa, ko da ma suna nan wani lokacin ya kan kirata a waya ya shaida mata, yau ma yana da bukatar fada mata abunda ya faru yaji nata tunani. He arrived in time a daidai lokacin da Momy ta kara Daddy ya shiga mota tana tsaye tana kallon yadda mai gadin gidan yake rufe gate, sai ta ya sake budewa da sauri jikin har bari yake, ashe Aliyu ya hango tafe. Murmushi tai domin ta san a duk duniya Aliyu kadai ya isa ayi masa haka a gidanta, baya danna horn sau biyu kuma bayana son jira saidai a jira shi, idan kana son kaganin bacin ransa ka kwada bata masa lokaci ko kuma saka shi jira na rashin dalili. Tana ta kallon dan na ta har ya faka motarsa a inda ya fi masa soyuwa a harabar gidan sannan ya fito fuskarsa ba yabo ba fallasa kamar kullum ya doshi inda mahaifiyarsa take, yadda yake takawa sai ka rantse da Allah takun kasaita ne da nuna isa, alhalin haka tafiyarsa take, kamshin turarensa na ta sanarda zuwansa tun kan ya karaso kusa da ita. Zai da ya rage sauran taku shida zuwa bakwai tsakaninsa da ita sannan ya dabbaka sunnar nan ta murmushi wacce ta kara mishi kyau da haifa. “Na ga Daddy ya fita yanzu har mun gaisa da shi ma” “Eh yana ta sauri za su je meeting” Haka suka jero ita da danta suka shigo cikin falon suna wannan hirar. Saman cushion ta zauna tana nuna masa dinning. “Ga ragowar breakfast can idan zaka ci kanenka suka raga” Ya dan yamutsa fuska yana murmushi dan yasan zolayarsa kawai Momy take. “Momy kin san ai bana cin ragowar kowa ni, ina Sisters” “Duka suna school” Ajiyar zuciya ya sauke wanda yasa Momy sake dubansa. “Wani abun ne?” Ya jimm na wani lokacin sannan sannan ya kalleta a natse ya ce. “Momy kin san kwana ki ina ta neman mai aiki ko? Sai ga wata yarinya ta zo gidan neman aiki.... ” Tun daga lokacin da Ataa ta zo gidan ya jera mata labarin har ya isa zangon da ya fi rikitar da shi. Da mugun mamaki Momy ta kalli. “Kuma ba ka ji komai a ranka ba Dan wajen Fulani? Ba zuciya da jini ne a kirjinka ba? A zalinci wata ta dalilinku har ka tsaya neman hujja?” “Amman ni ban ce a zalince ta ba?” “Miyasa da aka kawo maka kodar baka bincika daga inda ta fito ba? Akan me zaka zuba kudi mai yawa ka ce a samo maka kodar? Ba kayi tunanin ganin kudin zai iya saka Doc Asim aikata komai dan ya samu kudin ba? Ai da tun farko ka samu mai kodar ka yi magana da ita da bakinka, yanzu ga shi ka raya matarta kana cikin farinciki, ita kuma ka jefata a damuwa da bakinciki? Ka ji tsoron addu'ar wanda aka zakinta, kuma ka ji tsoron Allah ya isa, domin idan bata bi jikinka ba, tana bin dukiya da kaddara” Lumashe ido yai ya bude yana fusar iskar bakina a hankali. “Ka tuna lokacin da aka ce maka Rahma zata iya rasa ranta idan ba mata wano dashen kodar ba? Ka tuna? Ka auna ka ji ya yarinyar nan ta ke ji? Ita da mahaifiyarta ce, kamar ni ce ko Fulani aka cirewa koda ba tare da saninka ba? Idan ka gano me zaka yi?” “Zan yi duk abunda zan yi na kwato muku hakkinku” “To sai aka samu akasi ita yar talakawa ce, bata da wannan ikon bata da wannan gatan, mahaifiyar tana raye ko ta mutu babu wanda ya sani, wane hali suka shiga bayan wannan babu wanda ya sani, ina jiye maku tsoron abunda ta zai biyo baya, amman gaskiya an zalinci yarinyar nan” “Momy kin san inna sani ba zan zalince ta ba, na yarda bana kula kowa amman bana zalintar kowa?” “Ka bude zuciyarka kai tunani... Na san kana son matar ka kuma zaka iya komai akan samun lafiyarta, amman ina son na fada maka wani abu, ka ji tsoron addu'ar wanda aka zalinta, kuma ka ji tsoro mutumen da zai ce ya barwa Allah Allah shine zai isar masa, hakan yana nufin babu komai tsakanin shi da kai Allah ne zai wakilce shi ya fidda masa hakkinsa akanka.....” Kallon Momy yai zuciyarsa cike da tsoro da be taba jin irinsa ba, jikinsa yai mugun sanyi, tsoron abunda zai biyo baya kamar yadda Momy ta ce yasa zuciyarsa rauni... _____________________ Page daya ya rage mana mu gama free pages In-Sha-Allah. if you want to subscribe pay 300 to 0314795884 Abubakar Hadiza Gt Bank. sai ku turo shaidar biyan wato screenshot ta wannan number 08036126660, ko kuma katin mtn na 300 ga marasa account ta wannan number 08036126660. yan nijar za ku tura 500fc na line Orange ko Airtel ta number nan +22790165991 sai ku min magana ta wannan number 08036126660 Za'a saka ku Group. Thanks 🙏🏻 Ku ziyarci YouTube channel dina, ku danna min subscribe kuma kui sharing. 👉https://www.youtube.com/channel/UCpAkml0pIh6MUnzt9nLh_qQ *Z A K I* By Khadeeja Candy 1️⃣5️⃣ Ya dade a gidan Momy zaune gaba daya jikinsa ya gama yin sanyi, yana ta jin kamar akwai laifinsa a cire mata kodar da akai, and if da laifinsa ya akai laifinsa ya shiga ciki bayan shi idan ma ba yanzu ba be tana ganin yarinyar ba, idan yai duba ta wani bangaren yana ganin cewar ba shi da laifin komai, shi dai kawai matarsa yake nemawa lafiya and shi be ce a cire da karfi ba. A masallaci yai sallah magariba sannan na ya dawo cikin gidan, jikin ba kwari kusan sai ya rantse shi be taba jin jikinsa a wannan yanayin, wata kila saboda ba a taba cutar wani a gabansa ba, ko kuma shi din be taba cutar wani da dukiyarsa ko da ikonsa ko karfinsa ba, sai wannan karon, duk kuwa da kasancewar wani bangare na zuciyarsa na fada masa cewar ba shi da laifi. Yana shigowa falon Sisters dinsa sika make kyam kamar babu wani abu mai numfashi a falon, ko wacce ta shiga natsuwarta, tsayawa yai kallonsu kamar yadda ya saba idan ya shigo cikin gidan domin lura da yanayinsa da kuma halin da ko wace daga cikin kannen nasa guda hudu suke cikin. “Ina Umar?” Ya tambaya da irin fuskarka nan ta ba wasa. “Be dawo ba” Duka su hudu suka hada baki gurin bashi amsa dan sun sani sarai baya son kyaluwa, Momy zata iya tambayarsu abu su tsaya tunani ko wani sha'anin kamin su ba da amsa amman ban da Aliyu baya daukar wannan shashancin a time din da ya tambaye ka time din zaka ba shi amsa, idan kuma kai kuskure wani abun ya fito daga bakinka kuma kai ne a matsala. Juyawa yai ya shiga dakin Momy sai ya same ta zaune saman carpet tana jan carbi. Guri ya samu kusa da ita a kasan ya zauna yana fiddo wayarsa. “Dan waje bata Fulani ina ta tunani anya likitan nan Asim zai kyale ta kuwa?” Dagowa idonsa daga jikinkin screen din wayar yai ya kalleta. “Ban gane ba?” “Ina tunanin kamar ta jefa kanta a matsala ne, baka tunanin zai iya yi mata wani abun da nan gaba ba zata sake shaidarsa ba? Babban likita mai asibitin kansa kamar Asim ba zai dauki wannan matsalar ba, ba zai yarda ta karya masa aiki ba” Aliyu yai shiru yana nazari. “Wannan abu be min dadi ba sam Wallahi, saboda ban jidadi abunda ya faru da yarinyar nan ba, duk kuwa da ban santa ba, amman na san irin zafin da ake akwai ace an cuce ba gashi baka da hali jan hakkinka” Mikewa yai tsaye yana fitarsa numfashi a hankali ya ce. “Momy zan tafi gida, na san yanzu Rahma ta farka” “To ka gaisheta” “Za ta ji” Ya juyo yana tafiyarsa kamar yadda ya saba har ya sauko kasa, ya nufi gurin motarsa yana shiga yai mata key ya dauki hanyar gidansa. Yana tafe yana tunanin abunda ya faru da kuma maganar Momy, he find himself in middle of tausayin Ataa da yarda cewa an zalince, every words of her yake tunawa da yadda take furta su, idan har ba zalince ta ba, ba zata iya daga hannunta ta mari babban mutun kamar Doc Asim ba, yadda ya lura da rashin tsoron da ke cikin idonta a lokacin da idanuwansa suke yawo a fuskarsa, ya tabbatar ko kashe Doc Asim zata iya yi a gaban kowa, and Momy was right ba lallai ne Doc Asim iya kyaleta ba. ‘Allah ya isa’ Haka maganarta ke ta dawo masa sabowa a kunne, ga wa zai isar mata, ga Doc Asim ko ga shi ko kuwa ga su dukansu? Haka yai ta saka tunani kala kala har ya isa gida, yai mamakin ganin Motar surikinsa a wannan lokacin, the first thing that come his mind is ko ciwon Rahma ya tashi ne, amman kuma idan ciwon ta ne ya tashi ai shi zata kira ba Daddynta ba. A bude ya samu kofar falon tun ka ya shiga yake jiyo muryar Alhaji Nasiru Gobir. Da sallama Aliyu ya shiga, surukinsa da wani yayan Rahma suka amsa masa, Rahma kan ko inda yake bata kalla ba. Gurin ya samu kusa da ita ya zauna yana kallon Alhaji Nasiru Gobir wanda fuskarsa ke dauke da damuwa. “Rahma ta fada min abunda ya faru, daman ta fadawa mahaifiyarta tun a waya, wannan wace irin yar iskar yarinya ce marar tarbiya haka?” Aliyu ya juyo gefensa ya kalli Rahma sai kuma ya sake kallon mahaifinta ya ce. “Ba ta fada maka abunda akai wa yarinyar ba?” “Ko ma mi akai mata ai ba mu muka ce ta siyar da kodarta ba, irin talakawan nan da kake gani Aliyu ba su da komai a ransu sai hassadar nai arziki, idan suka ganka da arziki ji suke kamar su kashe ka su kwashe dukiyar, shiyasa tsakaninmu da talaka aiki kawai mu biyashi, wata banza a banza bata isa ta shigo har cikin gidanki ta fada miki maganar banza ba, watan ma kuma talaka!” “Daddy har da kai ta ciwa mutunci, wai a gidanka ta raba ka koreta ni da kai duk ba musan darajar talaka ba” “Zan sa a binciko yarinyar da iyayenta sai na nuna mata ruwa ba sa'an kwando ba ne” Duk abunda ake Aliyu ba ce uffan ba, har Daddy yai musu sallama ya fita, a lokacin ne Rahma ta tashi ta nufi dakinta, shi kan sai da yaji tashin motar surukinsa sannan shima ya mike tsaye ya bi bayan Rahma. Gaban madubi ya same ta zaune tana cire dankunnen da ke kunnenta, kusa da ita yaje yai mata kissing sannan ya zauna gefen gadon yana kallonta. “Miyasa za ki kira Daddy ki fada masa maganar da bata kai ta kawo ba?” Da mamaki ta kalleshi “Wannan abun ne be kai ya kawo ba? Yarinya karamar yar talakawa kamar wannan ta fada min magana son ranta ka ce be kai ya kawo ba? Aliyu ka san me kake fadi kuwa?” “Amman ai zalintar ta akai? Yanzu kuma sai ki fadawa Daddy bayan kin san zai iya daukar wani mataki?” “Amman mu muka zalince ta? Daman can matakin na ke son ya dauka shiyasa na kira shi na fada masa, tun da kai ka kasa komai sai ma rike min hannu da kai dan kar na dake ta” “Sanadinmu aka zalince ta, kodar mahaifiyarta aka cire Rahma aka dasa miki? Kuma kike tunanin ba zatai wani hargagi na huce haushinta ba?” Juyo tai gaba daya ta kalleshi da kyau. “Kana magana Aliyu kamar ba kai ba? Lafazin da ke fitowa daga bakinta yana karantar da ni cewar ba kai ne ba?” Hannu ya kai ya kama hanyayenta ya cigaba da mata magana a hankali kamar yadda yake mata dazun. “Dear, zan iya juye yi wa mutum komai amman ban da zalinci, an riga an cuci yarinyar nan, kuma kodar nan an dasa miki ita wannan kadai ya isa yasa jin tausayinta waya sani ma ko mahaifiyar ta mutu” “Tausayi Aliyu? Tausayi? Tausayi fa ka ce? Mi mukai mata da har za mu ji tausayinta? Mu muka zalince ta ne? Akan mi zaka yarda da yarinyar daka soma gani cikin kwana biyu, saman da likitan daya saba yi maka aiki shekara da shekaru? Ban taba ganinka cikin wannan yanayin ba Aliyu, ba ka taba ce min na ji tausayin wani ba, baka taba ce min kana tausayin wani ba, wanin ma talaka irin wannan yar shekara a gidanka” “Ba tausayinta nake ji ba, ina kallon abunda akai mata ne a matsayin zalinci, and be dace ki saka Daddy a wannan maganar ba, zai iya unkura yi mata wani abu sanadinki, ni fa na yarda da wulakanta kowa na ci mutunci kowa kuma na kyama ci kowa amman ban yarda karfin iko ko dukiya su saka na zalinci wani ba, ba zan iya da hakkin wani a kaina ba” Kai ta girgiza masa tana murmushi irin mai ciwon nan idonta na cika da hawaye. “Ban taba yin wani abu ka ce ban yi daidai ba sai yau, ban taba daga hannu da sunan dukan wani ba ka hana ni sai yau, wani be taba fada min mummunar magana a gabanka ka kyaleshi ba sai yau, na fahimcin inda ka dosa Aliyu, ta wanke fuskarta kaga tana da kyau tana da fari tana da gashi na fahimta...” Mikewa tai tsaye zata fice daga dakin tana share hawayen da suka zubo mata, sai yai saurin rumgumeta ta bayan ya dora kansa saman wuyanta. “Ba kyau ba ne matsalar, ina auna irin halin da na samu kaina ne a lokacin da aka fada min cewar za ki iya rasa ranki idan ba a canja miki koda ba, na ji tsoro sosai Rahma, kullum fargabata kar na rasa ki, na shiga damiwa sosai wanda hakan yasa na fadawa Doc Asim ya samu ko koda ta nawa ce zan siya, amman ban san cewa zalintar wata zai yi ya kawo min ba, ni kenan da nake tsoron rasa mata ina ga ita da take tsoro rasa mahaifiya tana da daraja ga yayanta Rahma ko da kuwa talaka ce” “Babu ruwanmu da rayuwar wasu, abunda muke so shi muka samu, whither ya zalince ko mu muka zalince ba matsala ba ce, tun da mun samu abunda mu ke bukata, Aliyu bana son na sake jin maganar yarinyar pls” Juyowa yai da ita ta yadda zata fuskance shi irin fuskartar da zata famince ko wace kalma da zata fito daga bakinshi. “No ba haka ya dace ba, idan har ba mu bata hakurin zalincin da akai mata ba, be kamata ba, be kamata mu kara mata da wani abun ba, Daddy zai iya yi mata wani abu, and maybe Doc Asim ma ba zai kyaleta ba” Kallonsa take tana ta kokarin fahimtarsa amman sai ta kasa, zuciyarta nata raya mata cewar Aliyu ya fara son yarinyar nan ne, hawaye ne suka shiga nata zirya ta fasa cewa komai, ganin hakan yasa shi saka bakinsa cikin nata ya tsotse bakinta tas sannan ya matso da ita baya suka zauna bakin gado ya rumgume ta. ATAA POV. Tunda aka tsayar da maganar zuwa aikina Abuja na fara koyon wanka akai akai kamar yadda Maman Salma ta fda min cewar Abuja ba a kazanta, baa gulma ba a wasa duk abunda ya kai mutum shi yake yi, wani lokaci a rana sai nai wanka biyu ma, wankin baki kuwa ba a magana, akai akai na ke saka gawayi ina wanke bakina gudun kar na je ace yana wari, yadda na ke ta jin labarin Abuja a gurin Maman Salma sai ji duk na gagara na je kamar wacce zata je wani guri gurin jindadi ba aikatau ba. Sai duk wannan zumudin da murnar da nake idan tuna cewar zan tafi na bar Nana sai hankalina ya tashi na ji babu dadi, duk kuwa da nasan cewar ina bukatar aikin, kuma idan har na daure nai na san zan samu kudi kuma, kudin za su mana amfani sosai. Sai kullum Nana cikin nuna bata son tafiyata take, tana ta ganin kamar idan nai nisa da ita zan dawo na tarar ta rasu ne. Ana saura kwana biyu mu tafi Abuja kamar yadda Maman Salma ta fada mana, na shirya ni da Farida na raka ta bayan unguwarmu gurin kitso, ba mu dawo da wuri ba, kasancewar mun tararda mutun hudu suna jiran kitson, ga shi idan muka hadu da Islam mai kitso abun ba dama gurin fira da dariya, muna hanya ana kiran sallah la'asar muna tafe muna fira har muka iso gidan sai dai yadda na tararda gidan wan wulgar mana da kayan dakin Nana ya sa ka gabana faduwa, a tunanina ko mahaifiyar Farida ce tai mana haka domin bata son zaman mu a idan, yana daya daga cikin abun ya saka na ke son na samo kudi ko dan mu tashi mu bar mata gidan. “Muna zamanmu Malam zai janyo mana masifa, ai bari ya dawo sai ya san matakin da zai dauka tun wuri dan ni ba zan yarda da zaman mutanen nan a cikin gidan nan ba, wannan iskanci har ina?” Irin kalaman zagi da na ji suna fitowa daga bakinta ya saka na fahimci ba daga ita har ba ne. Da sauri na nufi dakin da Nana take ciki sai na sameta ta zaune tana kuka. “Lafiya Nana miya faru?” “Wasu mutane ne suka shigo cikin gidan nan suna nemanki, aka nuna musu ni saka ce na fada miki karki sake zuwa ki fadawa Rahma wata magana marar dadi, idan kika sake sai sun wulakanta ki, wacece Rahma kuma?” Ta karasa tana tambaya ta. “Matar da ta koreni aiki ce” “Fada kuka yi?” “Kawai dai mu samu dan sabani ne, ta ce talaka ni kuma na fada mata bakar magana” “Ataa dan Allah ki kama kanki, kin ga dai ke ba yar kowa ba ce, kar ki janyo mana wata matsalar muna neman abunda za mu ci” “In-Sha-Allah ba zan sake ba, wacan din ma kuskure aka samu” “Ina son ki min alkawari idan kin je Abujar nan, duk abunda za a miki za ki yi hakuri ki hade, ba za ki saka shi a ranki ba” “Na miki alkwari Nana” Na fada ina sakar mata murmushi. Sannan na tashi naje na waje na dauko duka kayanmu tare da Farida na dawo da su dakinmu, ni da Farida muke ta zagin masu kudi da irin wulakancinsu, Mahaifiyarta kuma nata shigar musu wai idan ban musu wani abun ba ai ba za su zo har cikin gida su mana haka ba. Ni dai ban ce da ita komai ba, ni da Nana muna ta jiran tsammanin idan mahaifin Farida ya dawo ya kore mu ya ce mu bar masa gida, amman be kore mu, kirana kawai yai ya tambayi ba'asi sannan yai min jan kunne akan gaba kar na yarda irin hakan ta kara faruwa, na jidadin yadda yai mana daman sanin darajar talaka sai talaka dan'uwansa, ko da yake wasu talakawan ma basu san darajar talakan dan'uwansu ba kamar Maman Farida. A daren taliya na dafa mana, muka ci ni da Nana sai da muka koshi nas sannan muka kwanta bayan mun kashe kyandir din dake haska mana dakin duk dare, yau ma kamar yadda na sabawa kaima da tashi da wuri na tashi sai dai bayan na yi sallah asuba na koma na kwanta tun da bana aikin komai kuma ina da bukatar bachi. Ko da na farka ranata fito ko'ina kusan duk wani abun da ake saidawa na kari kama daga koko ko waina sun kare a lokacin sai dai na yamma idan anyi, dan haka na dimama sauran taliyar da muka raga ni da Nana jiya mu ka sake cinta da safe. Sannan na shiga nai wanka na fito na shirya cikin yadinmu na gado na rufe kaina kamar yadda muka saba yi idan zamu je bara, wannan karon har da gashin kaina na saki ya sauko har gurin mazaunaina, sannan na dauki dubu daya a cikin yan kudi da suka rage mana dan na siyo takalmin zuwa Abuja domin takalmina sun cinye daga kasa. “Ki siyo mana tuwon ruwa daga can (bula) da kuli da zogale sai mu yi kwado” “To Nana sai na dawo” Na amsa ina saka kafata na bar gidan, misalin sha biyu na rana na kama hanyar kasuwar yar murna, domin bana son zuwa tsohuwar kasuwa ko sabowa saboda cinkoson mutane, alhalin ba wani abun kirki zan siya ba, a kafa na tafi duk kuwa da irin nisan da ake akwai amman ina jin kamar hasara ne na biya kudin achaba bayan muma muna da bukatarsu, kara dai idan zan dawo sai na hawo achaba ko Napep na dawo shi ma idan na rago canji. Abun ka da wanda ya so tafiyar kafa, kuma gwanim tafiyar nan da nan na isa kasuwar murna, wata karamar kasuwa ce wance za a iya kiranta da unguwa ma domin mutane da yawa suna da gidaje a cikin kasuwar ba kamar sauran kasuwani ba. Daga bakim titi ma tsaya na siye takami na roba sai da natsaya na gwada wandanda suke yi ma kafata sannan na biya kudin dari shida da hansi, murna ta cika min zuciya domim rabon da na saka talkami mai tsada kamar haka har na manta duk talkamin da zaka gani a kafata ko dai an bani ne ko kuwa wasu sun gaji da amfani da su ne sun jefar na tsinta na gyara ina sakawa, kusan ma sai na ce ko a lokacin sallah da ake siyayya ni ba asiya min sabon kaya ba balle wani sabon takalmi. Bayan na bashi kudin na shiga cikin kasuwar na siyo abunda Inna ta aike ni sannan na fito na tsaya titi jikin wata mota ina jiran wasu motocin su gama wuce saina tsallaka na koma ta dayan bangare na hau Napep da naira hansin din da suka rage min. Ina kokarin tsallakawa wata motar na kokarin parking kusa da wance na ke tsaye sai ji nai motar ta ture ni da karfi har sai da na fadi zaune. Lambar motar kawai na kalla na gane cewar mutumenan mijin matar nan, wani abun isa yaga ya kade mutum amman ba zai iya fitowa ya duba waya kade ba, waya sani ko da gangan ya kade ni. Unkura nai na tashi na nufi inda yake na daki gilashin motar da karfi sai ya sauke gilashin yana kallona da cat eyes dinsa. “Me na maka za ka kade ni? So kake ka kashe ni? Wulakancin da ka tura aka mana a gida be wadatar da kai ba, sai ka kade ni? Kai wa wane irin mutum ne? Kana son matar ka kasa cire kodarka ka bata sai da kasa a zalince mu aka cire aka dasa mata, kuma yanzu dan tsabar zalinci na yi magana shine zaka aiko har gida a ci mana mutunci a wulakanta mu? Hakan bw maka ba yanzu kuma ka ganni zaka nemi wulakanta ni?” “Ba a nuna ni da yatsa” Shine kawai abunda ya fada yana hakimce cikin motarsa yana kallona ido cikin ido kamar ba da shi na ke masifar ba, ba dan cewar na ji maganar ba da sai na rantse ba daga bakinsa ta fito ba. Ni sai a yanzu na lura da cewar na nuna shi da yatsa din ma, a maimakon daya sai na saka yatsuna biyu na nuna shi da su. “Saboda kana wa? Mai arziki? Mai arzikin da ba zai iya zuwa gida da ko naira ba? Mai arzikin da bai iya komai da duniyarsa ba sai zalinci? An nuna ka ka yanka ma idan ka iya, bana tsoronka kai da muguwar matarka da mugun likitan nan, babu tsoronku babu kaunarku ko kadan a zuciyata” Ina gama fadar hakan na tofa masa yawu a motarsa na koma inda nake tsaye, na tsallaka titi ina ganinsa yana ta kallona har na tari achaba na na hau, shi da mutanen da suka fahimci fadanmu. Sam babu tsoronsu yanzu a zuciyarta ko kadan, sai ma tsanarsu da nai har na isa gida zuciyata zafi take saboda bacin rai. Sai dai ban fadawa Nana ba, kuma ban nuna mata cewar wani abun ya faru ba, ina shiga na shirya mana tuwon ruwan na gyara zogale na kwada mana muka ci, sannan na cigaba da shirye shiyena a yar ghana must go dita da na siyo sabowa. Bayan sallah isha'i muka kwanta ni da Nana, sai da na tabbatar ta yi bachi sannan na taso na baro mata dakin na zauna a tsakar gida cikin farin wata ina ta kallo taurari kamar mai kirgasu, tunani a zuciyata lallai ba dan talauci ba babu abunda zai nisanta ni da mahaifiyata. Kukana nai ni kadai babu mai bani hakuri har nai na gama sannan na wanke fuskata na koma dakin na kwanta amman bachi ya kasa daukata, sai na juyo da fuskata kusa da ta Nana ina ta kallonta kamar ance idan na tafi ba zan dawo ba. Tun kiran sallah fari na farka, domin maman salma ta fada cewar da na yi sallah asuba na zo mu kama hanya, ina sallah Nana na kuka har nai na gama, ina cikin yin addu'a aka buga kofar gidansu Farida na san ba zai wuce Maman Salma ba, a nan ni ma na fashe da kuka na kama hannayen Nana na rike ina ta shafasu a fuskata, Farida ta shigo dakin ta dafa ni tana ba ni hakuri. Sai na juyo na kalleta. “Ga Amanar Nana nan na baki, ki kula min da ita iya gwargwadon ikonki, ki yi mana gwargwadon abunda za ki iya, kin sani Farida ba dan talauci ba babu abunda zai nisanta ni da ita, tana da bukatata amman dole na tafi na nemo kudi. Dan Allah ki kula min da ita” “Na miki alkwari Ataa zan kula da Nana In-Sha-Allah” Na rumgume ta ina kuka kamar yadda ita ma take, sai kuma na sake ta ka saka hannayena na kama kafar Nana ina Shafawa. “Na yafe miki Ataa na yafe miki duk abunda ke tsakanina da ke, tashi kije Allah ya tsare ya kai ku lafiya” “Amin” Na fada sannan na mike tsaye ina kuka sosai na fito nai ma mamar Farida sallama da mahaifinta na karasa gurin Maman Salma sai wacce ke tsaye tana jirana, sau biyu ina waigowa ina kallon kofar dakin da Nana take, ina ta jin kamar kar na tafi na barta amman tafiyar ta zame min dole. Gidan Maman salma muka koma ta dauki kayanta a nan na gane cewar ba ni kadai zata kai ba, domin tare da yan mata shida muka kama hanyar Abuja bayan direba ya zo har gida ya same mu, da alama direbanta ne sun saba da juna ita da shi. Tafiya mukai ta yi, tun ina hawayen rabuwa da Nana har na soma wayewa, tafiyar ta fara ci min rai, a zariya muka tsaya muka karya sannan muka cigaba da tafiya mai isa, a takaice ba mu isa Abuja ba sai cikin dare... ALIYU POV. Yana rike da jarida a hannunsa amman ya kasa karanta komai, abunda Ataa ya fada masa jiya kawai yake tunani, wani be taba karfin halin fada masa magana mai zafi kamar ta jiya da Ataa ta fada masa ba, beside shi be san ya tura kowa gidansu ba, be ma san inda gidansu yake ba, and kadewar da yai mata ma bada gangan yai ba. Sai dai ko ba komai yadda take ta karfi hali ta burge shi, and yana da right din yi mata excuse tun da Azzalumi take ganinsa, kuma zalintarta akai? But waya tura wasu gidansu? Ko Doc Asim ne kamar yadda Momy take masa hasashen cewar zai iya cutar da ita? Ko kuwa mahaifin Rahma ne wanda shi ma yasan ba a zai kyale ba? Ko dai wanene he need to know ta dalilinsaba zai yarda sake zalintar kowa ba. Zaman da Rahma yai kusa da shi yasa shi dagowa daga dogon tunanin da yake ya kalleta yana kai hannu ya shafa gefen kafadarta. “Dear na gaji da garin nan, bana son mu sake neman wata mai aikin wani abun ya faru, kuma gidan nan zamansa da datti ni bana so kyankyami na ke ji” Be ce mata komai ba, daman can ta san ba zai ce ba. “Ni mu koma Abuja kawai tun a can komai yi mana ake” Ya aje jaridar hannunsa ya janyota jikinsa. “Ba yanzu ba” Da mamaki ta daga kai ta kalleshi. “Saboda me?” Shiru yai for like five minutes before ya bude baki ya ce. “We need to help her” “Who?” “Yarinyar da aka cirewa mahaifiyarta koda, zata iya shiga wani hadarin saboda mu, be kamata mahaifiyar yarinyar nan a jikinki ba, tana kallon mu a matsayin azzalumai, kuma ta rayu a cikin kallon zalintar za mu sake yi wani zai iya fakewa da mu ya zalince a again” Wani irin zaranannen kallo tai masa kamar ya ce mata za a cire kodar jikinta ne a mayarwa mahaifiyar Ataa.... ______________________________ Assalamu Alaikum. Kamar yadda na fada yau na kai karshen free pages wato page 15, nace 12 zan kare free pages wasu suka roki n kara na kara to 15. Masu niyar siya za su iya sending 300 to 0314795884 Abubakar Hadiza Gt Bank, sai ku turo shaidar biyan ta number nan 08036126660. Yan nijar kuma za ku turo 500fc ta number nan +22790165991 sai ku min magana ta number nan 08036126660 zan saka ku group. And for our yan kasuwa da suke son a tallata musu hajarsu it's 4k via 08036126660. Masu niyar siya da marasa niya duka Allah ya wadata mu da arzikin na halal. Thanks 🙏😍🌹 1️⃣6️⃣ A wani babban gida muka kwana da alama ta san mutanen gidan domin na ji sai tambayarta wasu suke tana cewa suna lafiya. Shayi da biredi aka kawo mana da safe muka karya sannan muka shiga bandakin mukai wanka da shower abun ban taba ba kuma na dade ina mafarkin yi. Bayan mun shirya aka sai ta waremu mu uku muka shiga motar da muka zo da ita, ni da wata Murja da Humaira.    Tafiya ake ta yi ni dai ban gane inda muka dosa ba, ban kuma zan iya cewa ga inda aka bi ba, domin akwai tazara sosai tsakanin unguwar da muka saka da kuma wance za mu je, har ya zamana da za ace na dawo da kaina ba zan iya ba. Sai dai abunda na kura da shi unguwar ta manyan mutane ce, domin manyan benaye ne a unguwar sai kuma wadanda ba benaye ba amman masu kyau sosai da daukar hankali, a bakin ko wane kofar gida an kawata shi da furanni, kuma babu kowa a unguwar sai manyan motocin alfarma da ke wuce shi ma jifa jifa. Ba dan na san halin Maman Salma ba da na zargi ko wani abun za a min a unguwar domin a rayuwata ban taba zuwa irin wannan unguwar ba, hasalima ban taba sanin cewar akwai irin wadannan manyan gidaje da benaye masu kama da ma'aikatu a Nigerian ba.   A bakin wani kato gate direban mu ya tsaya, yai horn, wani matashi mai siffar karfi da kuzari ya leko ya zo har gurin motar suka gaisa da Maman Salma sannan na koma ya bude mana gate din. Da muka shiga gate din farko sai na hango wani gate din a tsakanin tafiyar wacan gate din da na farko yai taku sittin bayan shi kuma akwai wani dan karami da aka kawata da furanni, banbancin gate na biyu da na uku na ukun irin wannan ne da aka saka kawai dan kwalliya wanda zaka iya hango na ciki na ciki kuma ya hango mai shirin tahowa, na biyu kuma be kai na farkon girma ba, na farko shine kato gashi dogo kamar yadda ginar gidan take.   A wani kato fili direban ya aje motarsa, yamma da filin an kafa wata katuwar rumfa mai kala wance ta lullube wasu manyan motoci da ban taba ganin irinsu a sokoto ba, da alama gidan kashi uku ne, bayan bangaren da ke fuskarta mai shigowa ga wani can yamma da motoci, kuma akwai wani arewa da motocin, gaba daya gidan da duk wani abu na kwalliyar gidan na glass ne, ya wasu furanni kananan da suka kara haska gidan, bayan wadancan na nesa da mu da na ke hangowa masu tsayi da hudu an musu yar karamar kofa, da alama Garden ne kamar yadda na ji ana fadar cewar gidajen masu kudi suna yin Garden, muna rufe motar sai ga barewa ta fito da gudu daga Garden din da kahoninta tana kallonmu kamin ta juya da gudu ta koma ciki. Tsuntsun maka ne Peacock har guda hudu ke ta yawo a harabar gidan yana bude fukafukansa abun sha'awa, wani irin shauki ne ya kamani da kuma tsoro a lokaci daya, domin irin manyan masu kudin nan ba su cika ganin kimar talaka ba, balle kuma ace za ka yi aiki a karkashinsu ne.   Daya daga cikin part uku da suke gidan muka nufa, Maman Salma na gaba muna biye har muka isa, gaban kofar ma duk furanni ne irin na kaskon nan an kawata katuwar kofar da su. Wani dan maballi ta danna taja baya ta tsaya jiran bude mata amman ba a bude ba, sai ta sake danna bayan wasu mintuna, nan ma sai da aka kara bata lokaci sannan aka bude kofar falon. Ba mu ga wanda ya bude mana kofar ba, da alama wanda ya bude komawa yai ya zauna a daya daga cikin manyan sofa din da suke katon falon mai kama da falo uku. Wani kamshin masu arziki da turaren mai tsada ne ya fara yi mana marhabun kamin ac da ke falon ya karaso garemu. Wasu manyan yan matane su hudu hakince saman kujera suna kallon wani kato tv wanda ban taba ganin irinsa ba tun da Nana na haifo ni duniya. Babu wacce ta juyo ta kallemu daga cikin yan matan balle ta amsa mana sallamar da muke, duk kuwa da irin daga mana hannu da Maman Salma take na alamar mu sassauta muryarmu.   “Hajiya Rukaiya da Hajiya Maryam ina kwananku?” Maman salma ta fada da dukan far'arta sai a lokacin ne yan mata suka dago suka kallemu, wacce na ke zaton ita ce Maryam din ta amsa a kaikaice tana mana kallo ba uku saura kwata, yayinda Rukaiya ta sakarwa Maman Salma Murmushi kadan, sannan wacce ta fi su kurciya ta dago ta kallemu sai ta maida kanta gurin zeeworld din da suke kallo. “Na ce ko Hajiya tana nan?” Maman Salma ta tambaya kamar da tsoro, sai wacce aka kira da Rukaiya dazu ta kalli karamar ta ce. “Baby je ki kira mata Mama” Da kamar ba zata je ba, sai kuma ta mike tsaye tana sanye da wasu guntayen kaya irin na turawa wato dogon wando da be kai kasa ba, da kuma t-shirt ta mata mai guntun hannu kanta ba dankwali an yi mata kitson attach tsorayen sun sauko har bayanta. Wata katuwar mattakala ta nufa irinta ta indiyawa mai fadin ta fara takawa a hankali har ta haye sama gaba daya, daya daga cikin dakunan da muke hange ta tura ta shiga. Shiru shiru bata fito ba har kusan awa daya sannan muka hango an bude kofar wata kasaitacciyar mace mai isa da ji da kai ta fito daga dakin tana sanye da wata dakankiyar shadda mai kamar kamfala sai shining take kamar an shafa mata mai. Da ďai-ďaya matar take takawa tana saukowa stairs din wani saurayi mai kama da ita na gafenta fuskarsa dauke da murmushi ya zuba duka hannayensa aljihu. “Mama ba ki yarda da ni ba” Saurayi ya fada bayan sun sauko tare yana kallonta. Uffan ba ta ce masa ba bayan hararar da ta watsa masa ta nufi wata one seater da ke fuskantar mu ta zauna, shi kuma saurayin ya zauna hannun sofar yana cigaba da gitse dariyarsa. Maman Salma ce ta fara mika mata gaisuwa ciki da girmamawa daga kasan tile din da muke zaune mu da ita. Sai Hajiyar ta amsa da far'arta kadan tana shigar da idonta can ciki a yayinda take kallonmu irin kallon nan na rashin ganin kimae talaka. “Lafiya Kalau Ramatu an shigo” “Eh Wallahi, dama na fada miki zan shigo ai” “Haka ne, suna wadannan yaran?” “Eh sune sai ki zabi wacce kike so, idan ma duka za ki dauka ga su nan dai” Maman Salma ta fada tana dariya. “Aa daya ta isashe mu,wanke wanke ne kawai sai shara da mopping da dan aikin da zai taso, kin san ni bana yarda yar aiki tai min girki, haka ma Ammy bata son girki” Ta fada tana daga hannu kamar bata son motsa jikinta. Ina dauke idona daga gareta na kalli d'anta sai na ga ni yake kallo kamar mai mamaki, maida kaina nai kasa na sake dagowa muka hada still ni yake kallo. “Mama kin ga kyau? Subhanallahi ahsanar halikin amman wannan yarinyar Allah ya miki kyau, you're so pretty” Ya fada yana kallona daga can inda yake zaune. “Mama wannan yar Fulanin za mu dauka tashin hankali” Ya sake fada yana kara kallo da kyau, wanda hakan yasa sauran yan uwanshi mata suka dago suka kalleni, a cikinsu babu wance ta ce ina da kyau suka maida dubansu gurin tv da suke kallo. “40k za mu biya idan ya miki” “Eh yayi Hajiya Allah amfana mana su, ke kuma kina da 30k a wata ni ina da 10k ya miki?” Maman Salma ta fada tana kallona da sauri na gyada mata kai da sauri zuciyarta cike da jindadi har dubu 30k.  “Bude baki ki yi mana na ji muryarki mana kyakkyawa” Saurayin ya fada yana kallona, sai Hajiya ta daka matsa tsawa tana kallonsa. “Muhseen what this?” Mikewa yai tsaye yana dariya ya nufi gurin da sisters dinsa suke zaune ya zauna. Sannan Hajiyar ta kalli Maman Salma ta ce “Ki fada mata yadda komai ya ke, sannan ki kai ta bangaren Ammy ta ganta kuma ta nuna mata aikin da zatai” Maman Salma ta juyo kaina ta nuna min Hajiya. “Wannan sunanta Mama Fulani haka ake kiranta, wacan dan ta ne Muhseen amman Ya Muhseen ake kiransa, wacan ma Anty Maryam za ki kirata, wacan Anty Rukaiya, wacce ta shiga daki dazun kuma Anty Baby, akwai wani na nan shi ma zaki ganshi Shi ma Ya Ahmad za ki kirashi, aikinki idan kin tashi da safe kamin kowaya farka saki zo nan falon ki share ki yi mopping ki goge ko'ina ki shiga kitchen ki wanke kayan wanke wanke ki goge, sai ki jira idan sun farka sun fito daga dakinsu suna karyawa sai ki shiga dakunansu da na Hajiyar ki wanke bathrooms ki share dakin ki goge ki kunna turaren kamshi, a can ma idan zan kai ki haka za ki yi, kuma idan akwai wani dan aiki za a kira ki ki rika” “Okay In-Sha-Allah zan yi duk yadda kika ce” “To taso muje can bangaren Ammy” Tashi nai kamar yadda ta bukata muka fita daga falon muka nufi dayan bangaren, komai irin na bangaren da muka baro ne ban ta kujera domin a can sofa ne a nan kuma cushion ne, banbancin wannan matar da wacan wannan tana da far'a da son mutane ita da yayanta sabanin wacan da ke da izza da nuna isa ita da yayanta. A lokacin da muka shiga falon duka yayanta su suka gaishe da Maman Salma sannan Hajiyar ta hana Maman Salma zama kasa. Bayan mun gasa ta gabatar da da aikin da aikin da zan yi kamar dai yadda tai min a wacan bangaren, sannan ta gabatar min da matar. “Wannan sunan ta Hajiya Husaina amman Ammy ake kiranta, wannan yarta ce za ki kirata Anty Zee, wannan kuma Anty Samira, wannan kuma Anty Batulu, wannan kuma Anty Inteesar” Ammy ta yi dariya tana shafa kan karamar yarta. “Ai ba sai ta cewa Inteesar Anty ba, Aai yarinyar ma ba zata wuce sa'ar Inteesar din ba, ya sunanki?” “Aisha amman Ataa ake kirana” Na bawa Ammy amsar da sauri, sai duk muka maida duban mu gurin kofar shigowa falon da muka ji an bude. Sauran nan ne na dazun da Maman Salma tace na kira da Ya Muhseen ya shigo fuskarsa da far'a kamar dazun, kusa da Ammy ya zauna yana nuna mata ni. “Ammy ya kika ga yarinyar nan kalleta da kyau dan Allah” Ta kallini kamar yadda ya bukata sai tai dariya. “Tana da kyau gaskiya” “Wallahi mugun kyau ma Ammy” Sai duk suka saka dariya ni kuma nai kasa da kaina, Maman Salma ta ce. “Iyeyenta jajayen buzayen nijar ne, bari ma ta cire Hijab gashi har gadon baya” “Kai iyakar kyau kenan amman Ammy ki ce tai magana mu ji muryarta, na rantse da Allah yarinyar nan ta ruda ni, kin san ni da son mace mai kyau kuma fara” Ya Muhseen din ya fada yana ta kallona, ni dai ban dago ba, har aka ci aka shude muka yi ma Ammy sallama muka baro shi can shi da ita muka dawo dayan part din na Mama Fulani kamar yadda Maman Salma ta fada min sunanta. A nan tai min jan kunne sannan ta yi mata sallama, sai Mama Fulanin ta dauko tufafi da turare ta mika mata da yan kudi da ba zasu kai 10k ba, Maman Salma na shirin fita Inteesar ta shigo dakin tana sanye da kananan kaya ta mikawa Maman Salma katuwar bakar leda wai in ji Ammy, Maman Salma ta karba tana godiya sannan ta fice, ni ko na bita da kallo ina ta jin kewar gida tare jin kamar na bita mu koma tare. ALIYU POV. Yadda yaga hankalin Rahma ya tashi ya sashi kai hannu ya rika fuskarta. “Ba abunda kike tunani ba ne, Momy ta yi min wadansu maganganu da na ke ganin dacewar abunda ta fada, kuma har ga Allah Rahma kin sa idan har Daddynki Ko Doc Asim suka cutar da yarinyar nan mu ne sila” “Taya za mu zama sila?” Ta tambaya hawaye na sauko mata, wani irin mugu zafi take jin zuciyarta na mata saboda zafin kishi, ita kanta bata taba sanin cewar tana da kishi kamar haka a zuciyarta ba sai yau, jin Aliyu yana zancen wata yasa har kanta sarawa yake, nan da nan jikinta yai zafi zzazzabi ya rufe ta, ta soma jin sanyi na sauko mata. Haka yasa hankalin Aliyu tashi sosai, da sauri ya daga ta zaune yana dubata. “Maganar da na yi ce ta saka ki haka? Ko ciwon ne ya taso? Tashi muje asibiti” Kai ta girgiza masa alamar ba zata je ba, mikewa yai tsaye ya ciro wayarsa kamar zai kira Doc Asim likitan daya saba dubata sai kuma ya fasa ya kira wani likitan dabam. Abun ka da kiran mai arziki nan da nan likitan ya iso, ya duba ya bata magani yai mata allura sannan ya tafi. A bayanta Aliyu ya kwanta ya rumgumeta ya Lumshe ido kamar mai bachi kuma ba bachi yake ji ba, har yanzu maganar Momy yake tunani, a idonsa kuma Ataa ke masa gizo lokacin da ta wanke fuskarta ta fito gashinta har a baya tana nunawa Doc Asim fuskarta dan ya gane ta. Sai a yanzu ya fahimce dalilin daya saka take shafa bakin abu a fuskarta da kuma nikab din data taba sakawa lokacin da ta so gidan, yana tuna duk wata haduwa ta su, tge first fasa mishi mota da tai wanda har yanzu be san dalilinta na yin hakan ba, ko dai ita ma ta tsani masu kudi ne kamar yadda shi ma ya tsani talaka? Ya tuna lokacin da take masa bara a jikin mota har rigarsa ta taba ta, ya cire rigar ya saka boot, irin kallon tsoron da ta rika masa ne ya dawo masa sabo, wanda har ta kasa janyewa daga jikin motar shi kuma ya kasa cewa ta kauce ya shiga motarsa sai da Nana ta janyeta, da tears din da suka cika idonta har suka zubo a wacan lokacin, yasan ta ji tsoronsa ne kamar yadda kowa yake jin tsoronsa amman duk da haka tana da karfin zuciyar tsaya ta fada masa magana mai zafi ba tare da tsoro abunda zai biyo baya ba, kamar yadda ta fasa masa mota ma, da kuma fadan da tai masa jiya, yace ba a nuna shi da yatsa har ta saka yatsa biyu ta nuna shi da su wai ita ga masifaffiya marar tsoro. Dan murmushi ne kadan ya bayyan a gefen fuskarsa, shi kansa bw ankaro da murmushin yake ba har sai da ya ji yana kokarin fadada, da sauri gusar da murmushin ya sauke ajiyar zuciya a hankali ya kai dubansa ga Rahma wacce ke ta bachi ya sumbanci saman kanta ya sauka daga kan gadon ya nufi downstairs, wayarsa ya ciro haka nan kawai yake son labartawa abokinsa Nasir abunda ya faru, he don't know why maganar take son damunsa. Misalin biyu da rabi Rahma ta farka, ta tunanin maganar dazun ta shiga bathroom tai wanka, har ga Allah ta ga mijinta a cikin yanayin da bata saba ganinsa ba, yai mata wasu kalamai da bata san shi da kula da su ba, idan ta tuna irin kyau Ataa kuma sai tsoro ya kamata, gaban madubi ta zauna tana kallon kanta, iya aunawa ta auna tabbas ita ma din mai kyau amman ko kadan bata kamo Ataa ba, wata kila Kyau Ataa ne ya rude shi har ya soma tausayinta yana ganin abunda akai mata ba a kyauta ba, ita a duk zaman shekara shekara shida da tai da shi bata taba jin yayi maganar wata mace ba, sai wannan yarinyar. “Ba rin garin nan za mu yi, kara mu koma Abuja inda ba ta ma can balle hankalina ya tashi, idan muka koma can ni kadai zai kula da ni sai aikinsa, amman nan wannan bakar Momy zata iya damunsa da maganar yarinyar nan, kuma zai iya son ta tunda tana da kyau, amman a can ai be ganta ba, kuma mun yi nisa da Momy ba wannan zancen, daman can na san ba so na take ba” Ta fada tana murzawa jikin expensive cream, sannan ta shafa turare da powder ta mike tsaye ta nufi wardrobe. Tana cikin daukar kayan ta juyowa ta kalli Aliyu da ya shigo dakin cikin kananan kaya. “Aliyu Abuja na ke son mu koma cikin satin nan, na gaji da garin nan” Magana take masa amman kwatakwata ba ita yake kallo ba kirjinta yake kallo yana hade yawu, kamin ya kai hannu ya shafata zuwa bayanta yana kokarin kwance tawul din. “Magana na ke maka fa” Be kula ta har ya kwance tawul din ya soma shafa jikinta. “Alwala nai sallah zan yi” Sai da ta fadi hakan sannan ya saketa ya matsa baya yana tsosar lips dinsa kamar mai shan sweet, har cat eyes dinsa sun soma canja kala kamar ba shi ba. “Ka ji ni Abuja na ke son mu koma, na gaji da garin nan” “Ki yi sallah sai mu yi maganar” Ya fada yana fadawa saman gadon kwance ya runtse idonsa yana shafa kyakkyawar fuskarka da dayan hannunsa, dayan kuma ya saka shi cikin kafafuwansa ya matse sosai, yana jin lokacin da Rahma ta kabbatar ta sallah ya bude idonsa ya tashi zaune, sai wayarsa tai ringing alamar kira, ganin Nasir yasa shi tashi ya fita daga dakin dan baya son yin maganar a gaban Rahma tun da ya kula da bata son hakan. Saman cushion ya zauna yana picking call din, “Ya?” “Daidai, amman Aliyu ya kamata ka dawo Abuja akwai aiki da yawa a nan, kuma kasan akwai abunda be yiyu sai an saka a kamfanin nan” “zan zo amman ba yanzu ba, akwai abunda na ke son yin?” “Akan yarinyar nan ne?” Aliyu yai shiru be ce komai ba, wanda hakan ya Bawa Nasir damar cigaba. “Yana da kyau ka tabbatar yarinyar nan ba ta cutu dalilinka ba, saboda kar abun ya zo yai ta damunka ko ya shafe ka” “Kawai dai bana son kallon da take min na azzalumi” “Ka bata hakuri to kuma ka fada mata gaskiya cewar ba da saninka akai komai ba, ko da nasan ba zaka iya ba” “Hakuri....” Ya maimaita, bayanin ma yana jin ba zai iya mata ba, sai dai ya saka wani yai nata ko ya rubuta mata a rubuce, balle kuma har kalmar bada Hakuri ta shigo tsakaninsu, abunda yake jin ya zama wajibi akansa kawa ya wanke kansa daga kallon azzalumin da take masa ne. “Amman kasan inda take?” “No” Ya bawa Nasir amsar a takaice sannan ya kashe wayar ya mike tsaye ya nufi upstairs... *Z A K I -it's not free, pay 300 to 0314795884 Abubakar Gt bank, then send the evidence via 08036126660* Ko da ya shigo dakin ya samu Rahma ta gama sallah tana kokarin tashi tsaye, haka ta dauki carpet din ta jefar gurin akwatinta dan bata iya ninkewa sannan ta aje. “Dear ina da ina Daddy ya ke gina gidajen da be karasa ba?” “Gurare da yawa wani abun ne?” Ta tambaya tana kallonsa sai ya zaunar da ita ya zauna a kusa da ita yana sakar mata murmushinsa kadan. “Da ina da ina?” “Akwai wani Clapperto road, akwai a ali akilu akwai a guiwa da sauran gurare, mi za kai?” “Ina son na duba mai girma ne sai na yi ma Daddy magana mu bude karamin kamfani da shi” “No Aliyu ni fa bana son zamanmu a garin nan, gaskiya ni Abuja na ke son mu koma cikin satin nan ma” “Ba dole ni zan zauna ba, zan saka wasu ne” Ya fada yana mata kiss sannan ya mike tsaye yana kallon kansa a madubi. “Idan kina son Abuja za mu ko, amman ni zan dawo na karasa wani aikin” “Fita za kai?” Ta tambaya tana mikewa tsaye “Yes fada min abunda zan zo miki da shi” Hannu ta kai ta raka rigarsa tana kallon cat eyes dinsa. “Aliyu ina za ka je?” “Momy ke nema na” Ya bata amsa kai tsaye, wanda hakan yasa ta sakinsa ba dan ranta ya so ba, domin zuciyarta ta fara yi mata zargi akansa, sai dai ba damar hana shi fitada kuwa karya yai mata tunda ya ambaci sunan Momy. “Bana son komai amman ka dawo da wuri” Ta fada cikin yanayin da ke nuna bata son fitar tasa. Sumbantar goshinta yai “Sure” Sannan ya juya ya fita yana wasa da keys din hannunsa. Gurin windows ta nufa ta tsaya daga can sama tana kallonsa har ya tashi motar aka bude masa gate ya fice, ajiya zuciya ta sauke zuciyarta na raya mata wani abu marar dadi, yadda ta ke ganin Aliyu yana maganar yarinyar kwana biyu ta soma rashin yarda da fitarsa, ta san ba abu ne mai sauki ya samu gabinta ba, ba kuma lallai ya tsaya neman yar talakawa kanar wannan ba, amman zuciyarta na raya mata cewar mijinta zai iya son yarinyar saboda kyauta. “Ba lallai ne ya so ba, nasan Aliyu baya son talaka, kuma ko da ma yana son ta da gaske idan na nuna masa bana so ba zai yi ba” Ta furta ma kanta a kokarinta na kusar da abun a zuciyarta, domin saukar numfashinta yake tarewa a duk sa'in da tai tunanin cewar Aliyu zai hada son ta da wata. “Wadanda ma suka fita arziki, tsabta kwalliya sun kula Aliyu amman be kula su ba, balle wannan yarinyar, shi kansa ya san ba sa'ar da zai kawo ma kansa wannan a zuciyarsaba ne” Wannan karon murmushi take tana fadin wannan maganar, kamin zuciyarta ta kawo mata wani tunanin na dabam. “Miyasa ya ke cewa ya kamata mu taimaka mata?. Saboda yana ganin kamar ta taimake ni na samu lafiya ne! That's it,” Wani shaukin son mijinta ne ta ji ya lullubeta, ta sani sarai Aliyu yana sonta baya son bacin raita kuma be hada sonta da son kowa ba, miyasa ma zatai wannan tunanin tun farko? Sai a yanzu take jin kamar ba ta kyauta masa ba, da tai tunanin zai iya son wata yar talakawa can kamar Ataa yar talakawa ma kuma yar aikin gidansa, ji tai kamar ta yi wani katon sabo, shi kansa ta san idan ta fada masa zargin da take masa ba zai jidadi ba, kuma zai yi fushi da ita. ALIYU POV. Clapperto road ya fi tsaya masa a rai, domin tana fadin sunan unguwar ya tuna da lokacin da ta fashe masa gilashin mota ya biyo titi sai gashi ya ganta ta shiga kangon gidan, sai dai be taba tunanin cewar mahaifin Rahma ne da gidan ba. A hankali yake driving dinsa har ya isa unguwar daidai inda yasan gidan yake ya tsaya, daga cikin motar ya yake kallon kwannon da aka saka aka zagaye gidan, kofar shiga gidan a rufe, hakan kawai ya samu kansa da kin son barin gurin, and baya jin zai iya fitowa daga cikin motarsa ya tambaye wani ina masu gidan ko abunda ya shafesu, yana daga cikin abunda ya tsana neman wani abu that's why sai dai ya saka a masa, but this time around yana jin kamar da kansa yake bukatar yin gudun kar wani yai masa fahimta baibai.   Sai da ya hango wani tafe kusa da motarsa sannnan ya sauke gilashin motar ya bude baki kamar baya son magana ya ce. “Malam ina masu gidan nan?” Mutumen da aka tambaya ya tsaya daidai gilashin motar Aliyu yana kallonsa ya ce. “Mai ainahin gidan kake tambaya?” Aliyu yai shiru na yan mintuna kamar ba zai sake cewa komai ba. “Wata fulanin yarinya na ke tambaya” “Oh Ataa buzuwa ga inda suka koma can, gidan na shiga kwanar akwai wani karamin gida ba sosai ba, ka tambaya suna can” Mutumen na gama yi ma Aliyu kwatan gidan da ke nesa da wannan, Aliyu ya daga gilashin motarsa ba tare da yai ma mutumen godiya ba, ba kuma tare da ya sake cewa komai ba. Har mutumen ya ji haushin bata lokacinsa da yai yana masa bayani. Inda mutunen ya kwatanta masa ya nufa amman ya ki ya shiga kwanar ya tsaya yana hangon gidan da yake sa ran shine mutumen yake nufi. Idan ma ya ganta mi zai ce mata? Shi ya fi tsaya masa a rai, yasa ba zai iya bata hakuri ba, and ba zai iya tsayawa yi mata bayani ba, then miye na neman inda take har ya nemi ganinta. ‘No idan na ganta da ido na tabbatar tana nan zan saka wani ya zo yai mata bayani, ba ni da hannu a ciki’ Zuciyarsa ta raya masa, gamsuwa da wannan yasa shi shiga kwana ya tsaya daidai kofar gidan, babu wanda zai aika ciki and wa zai ce a sallamo masa ma idan ya aika din? He decided ya danna horn idan an fito fine idan ba a fito ba kuma ya kama gabansa. Sau biyu ya danna kan yai na uku Farida ta leko ganinta yasa shi sauke gilashin motar yana aika mata da wani kallo. Tabbatar da kofar gidansu ake horn din yasa ta koma ta saka Hijab dinta ta fito ta nufo inda yake fake da Motarsa yana kallon kofar gidan na su. “Ina wuni?” Ya gyada mata kai alamar ya amsa gaisuwar gaisuwa sannan ya motsa bakinsa kadan ya ce. “Wata buzuwa na ke nema ance suna nan” Gaban Farida ya fadi, jin cewar Ataa yake nema, gashi daman daga ganinsa ba zai yi mutumci ba, abunda ya fara zuwa a ranta mi Ataa tai masa da ya zo nemanta, mi zai mata? Miyasa yake nema? Duk a lokaci daya tai ma kanta wannan tambayar. “Sun tashi daga nan” Ya sake kallonta kasa da sama ba tare da yace mata komai ta shiga masa bayani domin itama kanta tana jin kamar zai gano karyarta ne. “Eh mai wacan gidan ne ya ce sai sun tashi, saboda an fada masa maciji ya sari maman Ataa, da aka kaita asibiti suka dawo nan shine ya sa aka watsar da bukkarsu aka koresu ya zagaye gidansa, sai suka dawo nan shekaranjiyar nan suka koma Kaduna” “Ba su gida ne?” “Ba su da gida daman bukka ce suke kafawa da mutumen ya koresu suka zauna nan na kwana biyu sai kuma shekaranjiya suka koma Kaduna” “Kaduna wane unguwa?” “Na'am...” Tai shiru tana ta tunanin unguwar da zata fada domin ko a sokoto ba ko wace unguwa ta sani ba balle kuma a Kaduna da bata taba zuwa ba. “Rijiyar Zaki... ” Ya sake kallonta da kyau gashi fuskarnan tashi babu annuri duk sai tsoro ya kara kama ta. “Aa ba can ba unguwar mai malala... ” “Malali?” Ya gyara mata jin kamar ba ta fada daidai ba. “Eh eh can fa, kusa da wani gida mai jan gini zaka ga bukkarsu a gurin” Hannunsa ya saka ya dauko katinsa da ke cikin motar ya jefara kasa. “Ga kati nan idan kin samu labarin gaskiyar inda take ki aika min sako ta number, ko kuma ki tura min number ta” Dukawa tai ta dauki katin tana fadin. “Su da ke neman abunda za su ci ina ma zata samu waya, amman miyasa kake nemanta ta maka wani abun ne?” Ko ba ita ba be ji zai amsawa kowa wannan tambayar balle kuma ita da yake gani ita da banza duka daya. Gilashin motarsa ya tayar ya soma driving a hankali ya bar a gurin tsaye tana kallonsa har ta daina hangosa.    Daga Clapperto road ya dauki hanyar arkilla wato family house dinsu wajen Momy. Yanzu kan ya gane dalilin daya kai Ataa asibiti, wato maciji ya tsari mahaifiyarta a can ne Doc Asim ya ganta ya cire mata kodar, amman abunda ya fi tsaya masa a rai zancen bukkar nan, how on earth za ace akwai mutumen da be da gidansa kansa, even ma ace mutum be da gidan kansa ai akwai gidajen haya da zaka iya biyan kudi ka zauna, amman ya za ace a bukka suke zama, samun kansa ya kasa yarda da abunda yarinyar nan ta fada masa. A daidai gate din gidansu ya tsaya ya danna horn sau daya kan kace kwabo aka bude masa gate din ya shiga, a harabar gidan ya faka motarsa ya fiddo wayarsa ya kira Doc Asim, ringing daya ya picking a tunanin Doc Asim zai masa maganar ciwon Rahma ne ya ce ya tashi ko wani abun dabam amman a mamakinsa sai ya ji ya aika masa da wata tambayar ta dabam. “Yarinyar da ka cirewa mhaifiyarta koda miya kawo ta asibitin ka?” “Maciji ya tsari mahaifiyarta, suka zo bata da kudin magani ta ji ana zancen koda ta ce zata siyar” “Ba siyarwa tai ba Asim, cirewa tai da karfin tsiya, da siyar tai yi kudin da zaka bata za su isheta tai rayuwa na wani lokaci” “Ina shaidar siyar da ita da tai, kuma be kamata wannan ya dame ka ba, kai dai ka ce kana son koda kuma an samo maka ba an wuce guri ba” “Da na ce ka kawo min ban ce ka zalinci wata ba ai, maciji ya sari mamanta sai ki amfani da wannan damar ka yaudare ta ko? Mahaifiyarta tana raye ko ta mutu” “Ba ni da masaniya yanzu” Aliyu ya kashe wayar tare da bude motar ya fito, yana tuna lokacin da yake tare da kanwarsa Humaira har take mikawa Ataa hannu ta ce ta bata wayarta da ta dauka. Be samu kowa a falonsu ba, kai tsaye nufi dakin Momy da yake hangowa a bude, yana shiga ya sameta tana gyaran gadonta, da sallama ya shiga ya zauna a kujear da ke facing din gadonta. “Momy yau ke kike gyaran gado da kanki?” “To yau duk da wuri suka fita, kuma har yanzu ba su dawo ba” “Ai ba kullum za su rika aiki ba, su ma suna bukatar hutu, da dai kin samu mai aiki ai su ma sai su hutu” Zaunawa Momy tai tana kallonsa. “Shi gyaran gado shara wanke wanke girki har wani aiki ne? Idan ba su koya a gida ba so kake su je su yi ma mazajensu irin na matarka? Ai ba kowa ne namiji ne irin ka ba” Yayi murmushi. “Momy ita ma fa saboda ciwo ne, bata saba da wahala ba” “Kula da gida da miji shine wahala? Wasu na can Allah kadai ya san abunda suke kamin su samu su ci ma, wasu ba su kaita ba amman suna can sun iya kula da miji, kai yanzu baka san dadi mata ba sai ka samu mai kula da kai” “Rahma ma tana kula da ni Momy, ke ce ba ki gane ba” Tabe baki Momy tai “Dazu mun yi waya da Fulani ashe taje dubai har ta dawo ban sani ba, ta kirani tana ta min fada wai na dauke mata yaro” “Eh ta kirana kwanan baya tace min zata je dubai ashe tafiyar ba mai dadiwa ba ce, ai mun kusa zuwa Abuja Rahma ma ta fara min maganar” “Ya dai kamata kan ka koma gurin aikinka, kuma kasan Fulani ba son take kai nisa da ita ba” “Zan koma” Sai yai shiru for some minutes sannan ya kalli Momy ya ce “Momy wai ashe akwai mutanen da basa da gidajen zama har sun kashe bukka? I find it so hard to believe” “Ban fahimta ba, wa ya fada maka?” “Mamy yarinyar nan da na ke fada miki, wai ashe gidan da take zaune gidan baban Rahma ne, sai maciji ya sareta da ya samu labari sai ya koreta sanadin hakan aka kai mahaifiyar asibiti ina jin a can ne Doc Asim ya cire mata kodar aka sakawa Rahma, wai can din bukka suke kafawa su zauna” “Dan wajen Fulani ina ka samu labarin nan?” Momy ta tambaya jikinta a sanyeye. Sai yai shiru kamar baya son fadawa Momy cewar ya je nemanta ne. “Just tell me i want to help her, ina zan samu ganin yarinyar nan? An zalince da yawa, tana neman gurin zama ace kuma an yi ma mahaifiyarta haka, mahaifiyar ma tana da rai ko ta mutu? Kuma ace mutumen da ya koreta a gidan macijin ya tsareta a gidan an dasawa yarsa kodar mahaifiyarta, yarinyar nan ba zata taba mantawa da ku ba Dan wajen Fulani kun cucece ta” Momy ta fada hawaye na sauko mata, zuciyarta ta cika da tausayin Ataa duk kuwa da kasancewar bata taba ganinta ba ko sau daya. Aliyu ya baro kujerar da yake zaune ya zauna kusa da Momy. “Momy trust me, Wallahi ba da sanina akai mata haka ba, duk laifin Doc Asim ne, nima ta ba ni dan tausayi....” Momy ta kalleshi. “Da? Dan tausayi fa ka ce Dan wajen Fulani, sai ka ce ba musulmi ba, irin wannan yarinyar ai kamata yai ma a kwato mata hakkinta” “Gurin wa?” Ya fada yana kallon Momy. Sai ta share hawayen da suka zubo mata ta ce. “Seriously yarinyar nan ta ba ni tausayi, yarinyar da take irin wannan rayuwar sai kuma a sake jefata a wata rayuwar ta wahala, ku kuna cikin farinciki ita an saka ta a kunci” Ya busar da iskar bakinsa, ba dan tausayinta yake ji kamar yadda ya ce wa Momy ba, tausayinta ne gaba daya ya cika masa zuciya, be taba jin tausayin wata halitta mai sunan dan'adam ba kamar yadda ya ji yana tausayin Ataa a yau, and the most annoying part is be san inda take ba, waya sani ko sanadin hakan ta kara shiga wani halin. A unguwar yai sallah la'asar sannan ya nufo gidansa, yana ta sake saken zuwa kaduna daga can ya bi ta Abuja ya gaishe da Mama Fulani, sai dai daya tuna da cewar idan ma yaje din be san mi zai ce mata ba sai duk wani karfin guiwa na shi ya zube daga ya yanke shawarar samun wani ya bincika masa a can Kaduna din. ATAA POV. Ina zaune a inda Maman Salma ta tafi ta bar ni ban tashi ba su kuma ba su kula da ni ba, ina zaune a guri har na iya gane anyi sallah azahar ta hanyar agogon falon daya nuna karfe 2. Ban san wa zan yi ma magana ba cewar ina son nai sallah ba, domin ban ga fuskar kowa a cikinsu ba, duka yan matan ko wacce ji take da kanta dan ko kallo ban ishe su ba, bana jin cewar idan nai musu magana za su amsa min, ina zaune a gurin ina ta rokon Allah ya kawo min mafita sai ga Inteesar ta shigo sanye da uniform din Islamiya tana kallon inda na ke. “Ke Ammy na kiranki” Ta fada min sai kuma ta nufi Anty Maryam tana fadin. “Anty Maryam makaranta zanje yanzu ba kudin na siyo miki tuwon madara” Ni dai ban jira na ji abunda Anty Maryam din zata fada mata ba, na mike tsaye na nufi kofa na fita da sauri kamar zan fadi. Hanyar da naga Maman Salma ta bi farkon zuwan mu na bi na shiga part din Ammy da sallama, sai ta amsa min da far'arta kamar dazun har hakoranta biyu na makka na bayyana, na sake gaisheta ina risinawa kasa. “Lafiya kalau ya ma sunanki?” “Aisha amman Ataa ake kirana” “Masha-Allah ashe Mamana ce, fatar dai kin iya yankan allayahu ko?” “Na iya” “Da kyau to shiga kitchen gashi can sai ki yanka min ki wanke kinji ko?” “To amman ban yi sallah ba” Sai ta nuna min bandakin da ke falon. “Shiga can ki yi alwala” Na nufi inda ta nuna min, a lokacin da na shiga sai na samu komai tsaf kamar ba a taba shiga bandakin ba, a kasa nai alwala domin na hango akwai hanyar ruwa a gurin sannan na fito na shimfida dankwalina kusa da kofar bandakin nai sallah, sannan na nufi kitchen ina shiga na samu allayahu a kwando na dauka na gyara na saka wuka na yanka kananan sannan na wanke mata na aje kamar yadda ta bukata na fito daga kitchen din. “Na kare” “Yauwa sannu ko, za ki iya tafiya” Na juyo ina ta jin kamar nai zamana a part dinta ko ba komai zan fi sakewa fiye da part din Mama Fulani da ba su san darajar mutane ba. Haka na dawo part din cikin rashin jindadi da na dawo ban samu kowa a falon ba sai tv, a inda na zauna dazun na sake zama sai na raba da kujera saboda na jidadin jinginawa, haka na zauna a gurin har la'asar ba a bani abinci rana ba, da akai la'asar ne na unkura zan tashi sai na ji an turo kofar falon an shigo, waigowar da zan yi sai na ga Muhseen, murmushi ya sakar min ya karasa inda take nake yana fadin. “Tun da na ganki na ke ta tunanin inda na san fuskar nan take, sai yanzu na tuna da na taba ganinki asibitin uduth ko? Kin tuna?” Na dan yi shiru alamar tunani sannan na gyada masa kai alamar na tuna. “Good girl, ashe zan sake ganinki, kin ci abinci?” Na girgiza masa kai alamar ban ci ba. “To kin yi sallah?” Nan ma kan na girgiza masa sai yai murmushi. “Ba ki magana ne hala?” Na yi shiru ban ce masa komai ba, na yi kasa da kaina. “Za ki sha wahala idan kika ce kunyata za ki ji, ga toilet can je ki yi alwala sai ki zo ki ci abinci” Ina nufar inda ya nuna min sai Mama Fulani dake saukowa ta daka min tsawa. “Karki kuskura shiga toilet din nan, yarana su shiga ke ki shiga akan me?” Tsayawa nai cak ina kallonta kamar yadda shi ma yake kallonta. “Sallah za ta yi fa Mama” “Ko mi za tai taje can a tab din garden ta yi karta shiga mana toilet” Kamar zai sake cewa wani abu sai kuma ya kalleni ya ce. “Idan kin fita daga falon nan za ki ga wani gurin ai kin san Garden ko?” Na gyada kai. “To can za ki je” Na juya na fice daga dakin ina hangen yadda Mama Fulani take watsa masa harara da alama bata jindadin yadda yake min magana ne. Fitowa nai daga part din na nufi garden din, ina shiga na samu kaina a cikin wani irin katon guri mai shuke shuke kala kala ga wani bangare an ware anyi pool mai zubar da ruwa gwanin sha'awa. Inda na hango fanfo na nufa na kunna daya nai alwala na shimfida dan kwalina kamar dazun nai sallah, da nai sallah sai na yi zamana a gurin ina ta kalle-kalle kamar an ce na juyo sai na hango mutum ta windows mai gilass yana kallona, kasa nai da kaina ina jin tsarguwa da kallon wata kila ma ya dauki tsawon lokaci yana kallo ban sani ba. Tasbihi na shiga yi da hannuna ina tasbihi da na gaji na tashi na koma part din dan na fara jin yunwa sosai, ina ko shiga na samu su sukansu a dinning suna cin abincin, a inda na zauna dazun na sake zama na labe bayan kujera. “Yar kyakkyawa zo ki karba” Muryar Ya Muhseen ce hakan yasa ni lekowa sai yai kirana da hannu, ba musu na tashi na karasa inda suke sai ya miko min plate din abinci cike da nama. “Muhseen you know me well bana son haka, bana son wani ya ci abinci da kwannon da muke ci” Mama Fulani ta fada tana kashe ido. “Yunwa take ji” “Dan tana jin yunwa sai ta ci abincin a plate din ka? What nonsense is this? Ke tara dankwalinki ki zube, kamin a duba miki wani gurin” Mai nema sai hakuri, a haka na cire dankwalin kaina na aje akasa sannan na karbi abinci na zube a dankwalina yana ta kallona cikin yanayin da ke nuna be jidadin hakan ba, na dauka na fito daga falon gaba daya na koma garden na zauna na ci abuna sai da na koshi sannan na bude fanfan ko na sha ruwa na wanke dankwali na shanya. Ina gurin wani matashin saurayi dan kazo na zo ya same ni a gurin yana fadin. “Ke zo a nuna miki gurin kwananki” Tasowa nai na biyoshi yana gaba ina biye har muka isa gurin motocin gidan, wani tsohon gareji ya bude ya nuna min shi. “Nan za ki rika kwana” “To na gode” Sannan ya juya ya tafi ni kuma na zauna a gurin, ina ta kallon yadda yai datti, ba a dauki lokaci ba sai gashi ya dawo da tsintsiya ya bani wai na gyara gurin, haka kuwa akai na share gurin tas sannan ya sake dawowa ya miko min tabarma yai tafiyarsa. A gurin na shinfidata na koma part din Mama Fulani na dauko yar ghana most go dina na dawo dakin na aje, sannan na dauko dankwalina. A gurin an kwana har safe asubar fari na farka daman ban yi bachi kirki ba, sakamanon rashin abun rufe gashi garin da sanyi, garden din na nufa nai alwala na sake dawowa nai sallah. Ina gamawa na nufi part din Mama Fulani ina taba kofar na ji ta a bude na yi mamakin hakan ganin jiya da muka zo da Maman Salma sai da aka bude mana, kitchen na nufa neman tsintsiya ba dan na san tana nan ba, sai dan neman tunda babu wanda zan tambaya, ta can kofar fita daga kitchen din ta dayan bangaren na samu tsintsiyar da mopper na dauko na zo na share falon tas kamar yadda aka fada min sannan na fara mopping. Ina gaf da gamawa Ya Muhseen ya shigo falon yana sanye da Jallabiya. “Eyyy ashe jaruma aka kawo mana, tun da safen nan kike mopping” Na risina har kasa ya gaishe shi. “Ina kwana” “Lafiya kalau” Sai ya amsa min da kamar mamaki. “Amman tarbiyarki ta burgeni, ya sunanki ma?” “Aisha” “Ashe ki Mamansu Ammy ce, amman ke Fulani ce ko?” “Buzuwa” Na bashi amsa a takaice. Sai ya zauna saman sofa yana fadin “Kina makaranta?” Na girgiza masa kai. “Miyasa ba ki san karatu yana da amfani ba” “Na sani” Na bashi amsa a takaice zuciyata na sosuwa da tambayarsa, na san da ace ina da halin karatun da babu abunda zai kawo ni nan, kuma babu abunda zai saka Doc Asim ya cuce ni. “Ni nan da kika gan ni babu ruwana da karatu bana makaranta” Kallon mamaki nai masa kamin na ce. “Ka kare dai” “Aa ban kare ba ni ban taba yin karatun ba” “Likita ne kai fa” “Inji wa?” “Ranar da na ganka uduth da kayan likitoci na ganka kuma wani ya ce Doc” Ya dan wara ido. “Kai ashe kin iya gulma” Kunya ce ta baibaiye ni har na kasa sake daga kai na kalleshi shi kuma ya saka min dariya. Ni dai ban ji ta kansa ba har nai na gama na koma kitchen din na gyara na wanke komai na aje, ina kokarin ficewa sai gashi ya shigo ya nufi gas yana fadin “Kin iya amfani da gas ki dafa min Lipton?” “Ban taba ba” “Okay bari na nuna miki saboda wata rana, and wadacan plates din ba haka ake aje su ba, idan Mama ta gani zata miki fada gogewa ake sannan a jera” Shi ya nuna min yadda ake kunna gas din sannan ya nuna min inda kyalle yake na dauko na goge komai naje a yadda ya nuna min. A yadda na lura Ya Muhseen ne ya fita dabam da mahaifiyarsa da kuma yan'uwansa domin mutum ne mai son fira ga far'a ba shi matsala da mutane domin a jiya kawai da na zo gidan zuwa yau da safe na ji na sake da shi kamar na sanshi. Bayan na gama da falon na nufi falon Ammy ita na gyara mata, ko da na dawo part din Mama Fulani na samu duk sun fito daga dakunansu sai na sauki tsintsiya na nufi upstairs da zimmar gyara musu bedrooms dinsu sai Mama Fulani ta ce da ni. “Idan kin gama kije ki gyara part din Muhseen” “To” Na amsa a ladafce sannan na haye sama na tura dakin farko. 1️⃣6️⃣ *Z A K I -it's not free, pay 300 to 0314795884 Abubakar Gt bank, then send the evidence via 08036126660* 18. A hanyarsa ta gida ya kunna datarsa ya aikawa Nasir sako ta whatsapp. “Yarinyar an ce tana Kaduna unguwar Malali, ka sa a bincika min ita daga gobe, ka saka kudi a nemota” Yana rubutawa Nasir hakan ya aje wayar da a cinyarsa ganin Nasir din baya online ya cigaba da driving dinsa, a hankali yake tukin har ya isa gidansa, horn daya ya danna aka bude masa gate din, be shigo ciki ba sai ya tsaya a jikin gate din yana kallon katon gidansa, wani dogon numfashi yaja ya sauke yana kara duba tsarin gidan kamar wanda ya fara ganinsa a yau, maganar nan ta dazun ce ta tsaya masa a rai, how on earth za a ce wani be da gidan kansa kuma be da kudin da zai iya biya ya kama haya? Mai gadin ne ya zo gurin motar ya dan risina yana daga masa hannu. “Ranka ya dade lafiya dai?” Ya tambaya dan a tunaninsa ko shi yai masa wani abun da ba daidai ba. Kallonsa kawai Aliyu yai ya dauke kansa yaja motar zuwa harabar gidan yai parking. “Shiyasa take yin bara take wankin mota a titi aikin maza?” Ya furta yana fitowa daga motar, be san dalilin daya hana shi jindadi ba jin cewar su Ataa basa da gida har sun raba a wani gurin an koresu, he know be cika damuwa da sha'anin kowa ba but wannan ya tsaya masa a rai for no reason. “Zata iya jefa kanta a matsala saboda kyauta” Ya fada yana ta tuna fuskarta, dagon hancinta manyan idanuwanta masu kamar madara ga gashin daya gani a bayanta duk kuwa da kasancewar ba a gyare yake ba amman dai ya fahimci tana da long hair. ‘Ina ruwana da halin da zata jefa kanta, ni dai abunda na sani an cuceceta and ya kamata na fahimtar da ita abunda akai ba laifin mu bane that's all, babu ruwana da wani rayuwarta can be ma kamata nai wannan tunanin ba’ Sai ya ji kamar darajarsa ta rage taya ma zai yi wannan tunanin tun a farkon fari, rufe motar yai ya nufi kofar shiga falon wayarsa a hannunsa daf da zai shiga wayar tai vibration sai ya shiga ya samu kujerar da ta baya stairs baya ya zauna yana mayarwa Nasir da amsar sakon da ya turo masa. “Zan saka a bincika, amman Momy ta san da maganar kuwa?” “Kai dai ka saka a bincika kawai, idan an ganta ka fada min zan fada maka next abunda za ayi” “Za a bincika In-Sha-Allah” Thanks. Yana rubuta masa haka ya kashe datar ya mike tsaye sai ganin Rahma yai a bayansa idonta taf da hawaye har wasu sun fara sauko mata, saurin aje wayar yai a kujera ya zagoyo inda take ya dafa ta. “Minene?” “I was such a fool da na yi tunanin ba zaka iya son yarinyar nan ba, ashe ita kaje nema? Yanzu kuma ita za aka saka Nasir ya nemo maka? Why Aliyu? Kazamar yarinya kamar wannan” “No no no, haba Rahma yaushe kik fara munanamin zato? Ko zan yi soyayya da wata ai ba wannan kazamar ba, yar talakawa taya ma? Wallahi ba son ta na ke ba, kawai yarinyar tana bala'in ba ni tausayi ne, kuma kin ga sanadin mu an zalince ta be kamata mu kyaleta ba” “Ba mu muka zalince ba Aliyu miyasa ka kasa ganewa? Shi kansa Doc Asim ba zai zalince ba, ai ya fada maka ya bata kudi ita ce take son masa sheri wata kila ma hadin kai ne da ita dan ta bata mishi suna” Ya san duk yadda zai yi kokarin fahimtar da ita a yanzu ba zata fahimta ba, domin ranta ya bace sosai and ya san wani abu makamancin wannan be taba shiga tsakaninsu ba, ba lallai ne ta karbi abun a zuciyarta ba, musamman a yadda tai masa fahimta baibai,rumgume ta yai ya saka yatsunsa cikin nata. Ita kanta bata taba jin abu ya daki kirjinta ya ratsa zuciyarta yana neman numfashinta ba irin yau, ashe haka kishi yake, ashe haka ko wacce mace take ji idan mijinta na son wata? Bata taba samun kanta a cikin wannan yanayin ba sai yanzu, fashewa tai da wani irin kuka kamar an mata mutuwa shi kuma ya kara matseta a kirjinsa yana shafa bayanta, one of abunda ya tsana is kuka, kukan kuma ya zama shine silar musamman Rahma da baya son abunda ya taba ta. Sakinsa tai tana saka hannunta ta share hawayenta, sai ya mika dukan karfinsa ya rika ta a tare suka rika taka stairs din har ya shiga da ita dakinta bakin gadon suka zauna ita da shi, ta saka duka hannayenta ta rike masa riga hawayen na bin idonta. “Wallahi Aliyu idan ka so wata zan iya mutuwa, ba zan iya sharing dinka da kowa ba, ba zan so wata ma ta so ka ba balle har ka so ta i just can't” Tausayinta ne ya kama shi sai ya kara natsowa kusa da ita ya kai hannunsa ya rika fuskarta. “Babu kowa a zuciyata sai ke ke kedai, ba zan taba son wata dabam ba, ko da ba ki da rai ballantana kina raye, kina jin kin kyauta min idan kika kawo ma kanki cewar zan iya son wata yarinya kamar wacan yarinyar? Karamar yarinya kuma yar talakawa yarinyar da ta zo aiki a gidana? Haba Rahma ki rika tunani kamin ki yi abu mana you should trust your husband” “Tana da kyau amman” Ta fada tana yawo da idonta a fuskarsa. “Yes she's pretty amman ba hakan zai saka na so ta ba, taya wai zan so wannan yarinyar ai abunda ba zai taba yiyuwa ba ne, ki ma daina wannan tunanin kar mu samu matsala da ke” Ya fada yana tuna masa bacin ransa karara, dan har ga Allah da ba matarsa ce Rahma tai masa wannan zargin ba da ba zai dauka ba, shi be ga dalilin daya da zai saka shi son Ataa ba, daga kawai ya nuna tausayinsa sai Rahma ta kasa fahimtarsa, tausayinma da ba a zalince dalilinsu ba da be ga abunda zai saka shi jin tausayin nata ba. Cewar da yai yes tana she's pretty yasa Rahma jin kamar ya ce yes sai na aureta, at least ya yara kyauta ai abunda be taba ba, ko a tv suke kallo be taba kallon wata a gaban idonta ya ce tana da kyau ba, idan ya kama dole ya fada sai dai ita Rahma ya ce tana da kyau, domin kullum cikin yaba kyauta yake, amman a yau yace yes wata bayan ita tana da kyau and ita kanta da take mace ta san Ataa na da masifar kyau balle kuma Aliyu da yake namiji, bata jin nadamar sanin wani a rayuwarta kamar yadda ta ji na sanin Ataa ba, daman tana yawan jin cewar ba a son daukar an aiki kwace miji suke amman bata taba yarda ba sai yau, da tun farko Ataa bata zo aiki gidan ba, da Aliyu be ganta ba, har ta ga Doc Asim ta masa wannan kazafin da zai saka Aliyu ya tausaya mata. Yana rungume da matarsa har aka kira sallah magariba, sannan ya sake ta yana kallon fuskarta ya ce. “Zan je masallaci daga can zan mana takeaway okay” Ta gyada masa kai tana jin zuciyarta na yi mata yawo da wani abu marar dadi. Goshinta ya sumbata da alama sumbantar goshi yana cikin abunda ya fi kaunar yi a jikin mace, sannan ya tashi tsaye ya nufi kofar fita yana takunsa cikin kasaita kamar yadda ya saba, ita kuma ta bishi da kallo har ya fice, sannan ta tashi ta koma gurin windows ta cigaba da hangensa har ya kunna motar aka bude masa gate ya fice. Sallah ce kawai ta zame mata dole, ita a gaggauce tai yi ta kamar wacce ake jira ta dauki guntun veil dinta ta saka ta dauki makullin motarta ta sauka downstairs tana ta sauri kamar zata tashi sama, tun kan ta shiga motar ta fadawa mai gadi cewar ya bude mata gate, tana shiga ta fisgi motar kamar ba daga cikin gida zata fita ba. Arkilla ta nufa so take taje ta labartawa Momy abunda yake shirin faruwa dan ta san Momy bata san Aliyu yana ganin ya zalinci wata yarinya ba.   Ta isa cikin sa'a domin ta isa a lokacin da duka sisters din Aliyu suke falo Momy kuma tana dakinta zaune bayan gama sallah magariba, su kansu sun yi mamakin ganinta a gidan domin ba karamin abu ke kawo ta gidanba, sai idan za su koma Abuja ta zo bankwana ko kuma idan anyi wani biki ko gaisuwa rasuwa ko wani abun dabam. Cikin mutunci suka gaisa da ita dan haka suke daukarta kamar ba matar yayansu ba ko irin wasan nan na matar yaya da kannen miji bata yi da su, wai kar su rainata daman ta san family miji ba son matar dan'uwansu suke ba. “Momy na nan?” “Eh tana dakinta” Rahila ta amsa mata, sai ta nufi dakin da tana gyara veil dinta wai za a hadu da suruka, iyakar kokarin da tai na tara hawaye a idonta ne yadda Momy zata fahimci akwai damuwa a tare da ita, duk da yake a fuskarta kadai ya nuna tana cikin tashin hankali. Da sallama ta shiga tana maida kofar dakin ta rufe, Momy ta amsa mata tana aje wayar da ke hannunta tare da kallonta. Kusa da Momy ta zube zaune ta fashe da kuka, wanda hakan yasa hankalin Momy ta shi sosai. “Momy kin san Aliyu yana son wata yarinya yar talakawa wacce ta zo aiki gidanmu?” Jin hakan yasa hankalin Momy kwantawa daman can farko ta dauko wani abun ne na dabam ba wannan ba. “Yana son wata? Shi ya ce miki yana son ta?” “Ya ce ba sonta yake ba, wai tausayinta ya ke, wai sanadin mu aka zalince ta, ina tunanin karya take saboda ta san Aliyu baya son ya zalince kowa ne shiyasa ta ce haka, domin Doc Asim ya ce ya bata kudinta, amman Aliyu duk ya bi ya damu da ita har saka a nemo masa ita, Momy ace ya rasa wacce zai damu da ita sai yar talakawa? Ni shi ya komai bata min rai” Ta fada cikin kuka, Momy tsayawa kallonta tai, tun da take da ita bata taba tunanin cewar barin yau ta shirya taje ta gaishe da surukarta ba amman ta dauko kafafu ta zo ta kawo mata karar danta. “To shi dan wajen Fulani ce miki yai ba zai taba kara aure ba?” “Ba shine damuwar ba Momy yar talakawa fa, kaskantaccin mutane” “Yar talakawa ai ta miki amfani Rahma ba kodar mahaifiyarta ce a jikinki ba? Ko da siyarwa tai ballantana zalintarta akai aka cireta, talaka shi b mutum ba ne da kike kiranta kaskantacciya? Wannan wace irin magana ce?” Bude baki Rahma tai tana kallon Momy jin kamar maganar bata dame ta ba, a tuninta Momy irin Mommynta ce da bata son talaka wanda jin hakan zai saka ta hana Aliyu kula Ataa amman ga mamakinta sai ta ji wani abun da ba tai zato ba daga gurin Momy. “Wallahi Momy idan Aliyu ya ce zai so ta zan iya mutuwa” “To ki shirya mutuwa tun yanzu, domin Aliyu ba zai zauna da ke ke kadai ba, ko dan shi ma ya samu ganin nasa yayan, ko ba ita dole Aliyu zai kara aure ko dan Allah ya ba shi haihuwa, shekara takwas da aure amman har yanzu be haihu ba, ko ba dan haihuwa ba ai namiji ba zai maka alkawarin cewar ba zai kara aure ba ka yarda” Rahma ta kalli Momy hawaye na sauko mata zuciyarta cike da jin zafin maganarta. “Haihuwa na Allah ne Momy idan lokaci yai zan haihu, dan ban samu ciki a yanzu ba ba shi yake nufin ba zan haihu ba, komai na Allah ne” “Shi kuma talaucin ba na Allah ba ne ko? Yarinyar da kike raina wata rana za ki ga tayi arziki kamar ki ko ma ta fiki, kuma bari kiji na fada miki idan ma dan wajen Fulani na yawan fada miki cewar ba zai kara aure ba daga ke ki daina yarda, dan namiji haka yake anjima zai iya ganin wacce tai masa ya canja ra'ayi” Rahma ta kalli Momy tana ganin ta wulakanta ta ce wai wata rana Ataa zata fi ta, taya ma zata kai kamarta balle har ta fi ta. “Momy ko dai dan baki san yarinyar ba ne, wata kazama ce marar daraja, taya za ki hada ni da ita? Ni fa matar dan ki ce” “Da na hada ki da ita na yi sabo kenan? Ya yanzu kika gama fadin cewar haihuwa na Allah ba ne? Shi talaucin da arzikin ba na Allah ba ne? Ke bari na fada miki idan ma baki sani ba, arziki da talauci duka na Allah ne, wani lokacin talaka ma sai ya fika kima da daraja a gurin Allah, ba kwalliya ki ka yi wa Allah yasa aka haiho ki a gidan masu arzikin ba, ita kuma ba wani laifi tai ma Allah yai ta a haka ba” “Na yi zaton kema kin dauki ni kamar yar ki ne za ki share min hawayena shiyasa na kawo kukana a gurinki” Ta fada hawaye na sauko mata sannan ta mike tsaye ta dauki veil dinta ta fito Momy na binta da kallo. Haka ta fito hawaye na sauko mata amman bata damu da ta share ba, duk a maganganun da Momy tai mata ta fi jin zafin na haihuwa, taya Momy za tai mata wannan maganar kamar ba ta san Allah ne yake komai ba? Ta sani ita kanta bata da matsala Aliyu ma bashi da matsala so zata iya haihuwa a duk lokacin da Allah ya so. Amman bayan Mama Fulani a yau ma Momy ta yi mata gorin haihuwa. A maimakon ta koma gida sai ta wuce family house dinsu gurin Mommy ta da Daddy su da take ganin kamar sun fi kowa kaunarta a duniya, domin tana da tabbacin da su ta kaiwa kukanta tun farko da basu mata bakar magana kamar yadda Momy tai mata ba. Daf da kofar shiga falon ta faka motarta sannan ta fita tana hawaye har lokacin ta shiga falon. Mutane ta samu da dama a falon suna ta hidimar canja decorations din Falon ko ba a fada mata ba tasan Mai gidan Daddybsu ne zai zo wato Alhaji Bashiru Muhammdu Sarkin Agades, domin ta san a duk lokacin da zai zo sai Daddy ya saka an yi gyaran gidan, kuma an gyara masa masaukinsa, daman tun gobarar da ta faru be zo ba kuma be aiko kowa ya yi ma Daddy jaje ba, kasancewar Daddy yayi hasarar dukiya mai yawa a Shopping mall din nan daya kone, domin shopping mall din ya yafi ko wane kawo kudi kuma shi ne wanda kudin Daddy zalla a ciki ba da na mai gidansa ba.   Mommy na zaune a falon tana kallon yadda ake saka labulayen Rahma ta shigo yadda ta ga fuskarsa da ganinta a wannan lokacin ta san ba lafiya ba, hakan yasa hankalinta yai mugun tashi har ta kasa hakura ta kawo kusa da ita ta tashi ta tarbeta. “Ke lafiya?” “Momy Aliyu wata yake so?” “Wata yake so, wata wa? Waya fada miki” A nan ta narke a kasa ta fashe da kuka wanda hakan yasa hankalin Mommy kara tashi ta rikata itama tana fashewa da kuka. “Rahma ki fada min minene?” Daker tai shiru har ta iya zanawa Mommy abunda ya faru, sai Mommy rika hannunta suka nufi part din Daddynta, Mommy tai masa bayanin komai a take shi ma ransa ya bace musamman da ya ga yadda yar lelensa take kuka. A take ya daga waya ya kira Aliyu ya ce ya zo ya same shi a gida, ba a dauki thirty minutes ba sai ga Aliyu zaune a falon daddy daman he used to respect his in-laws da kuma iyayensa da matarsa duk abunda ya shafi nan baya wasa da shi.   Daddy ne ya fara kora masa da bayani kamin Mommy ta dora da nata cikin fada. “Be ma kyautu ace ka fara son wata ba Aliyu, kasan halin da Rahma take ciki idan kace zaka mata kishiya da wanne kake son ta ji?” Tun da suke maganar yake ta kallonsu har sukai suka gama sannan ya kalli Rahma ya ce. “Lokacin da zan aureki na fada miki cewar da ke kadai zan zauna? Na miki wannan alkawarin ke kadai za ki zauna?” Rahma ba tace komai ba sai kuka take, sannan ya kalli Daddy da Mommy ya ce. “Ciyar da yarku shayarda ita nema mata lafiya abu ne daya rataya a kaina, kuma shi ya kamata ku tuhume ni da shi idan ban mata ba, ba wai zancen karin aure ko kin sa ba, wannan abu ne da ke tsakanin ni da ita, matsala da za mu iya gyarata a tsakaninmu, ku hukunta ni idan na tsallake daya daga cikin abunda musulunci ya ce nai mata na take na ki nai amman ba wannan ba” “To rashin kunya za ka mana kanan ko?” Mommy ta fada tana watsa masa wani kallo kamar ba sukurinta ba. “Babu zancen rashin kunya a ciki Mommy, Rahma ta yi ba daidai ba kamata yai ku fada mana ku nuna mata abunda tai ba daidai ba ne, ba wai ku kirani ku tsare kamar haka ba” Daddyn kan mamaki da kataici ya hana shi cewar komai sai wani kallo yake watsawa Aliyu ta cikin gilashin idonsa, ya manta da cewar Aliyu mai arziki ne dan mai arziki dan gin amsu arziki, da dai ace talaka ne yake auren yarsu da za su iya juya shi yadda suke so amman ba mai arzikin da baya jiran abun hannunsu kamar Aliyu ba. Jin babu wanda ya sake cewa komai yasa shi kallon Daddy ya ce. “Akwai wata matsalar ne bayan wannan?” “Lallai Aliyu wuyanka yai kauri wato ita wannan ba matsala ba ce ko?” Daddy ya fada, Aliyu dai be ce komai ba sai kallon Rahma yake da idon da ke nuna ya fusata sosai. “Daddy ka bar shi kawai zan yi magana da shi” Rahma ta fada tana dagowa daga jikin Mommy ta dake kokarin riketa. “Babu inda za ki bishi yaje yai ta cusa miki bakinciki a zuciyata ya akashe mana ke da ranki” “Aa Mommy zan yi magana da shi, daman ban yi magana da shi ba ne na fada muku, idan abun ya gagara zan...” Sai kuma tai shiru bata karasa ba, tana tsoron kar ran iyayenta ya bace su hanata komawa gidan sahibinta ko wata matsalar wacce ta fi wannan ta shiga. “Sai da safen ku” Aliyu ya fada yana mikewa tsaye ya fice daga falon, da sauri Rahma ta bi bayansa wanda hakan yasa ran Mommy baci son tai ta riketa a gidan har sai Aliyu ya gane kurensa. A tare suka iso gurin motarsa Rahma na ta kallon fuskarsa ko zai kalleta amman be kalleta har ya bude motarsa ya shiga ya danna horn aka bude masa gate ya fice ya barta a gurin tsaye. Da sauri itama ta shiga motarta ta bishi ko da ta isa gidan ta samu har ya shiga dakinsa yana kokarin cire tufafin jikinsa. Jikinta a sanyaye ta shiga dakin tana ta kallonsa amman ko inda take be kalla ba, har ya cire tufafin ya daura tawul ya shiga yai wanka ya fito tana a gurin zaune, so take ta masa magana kuma bata san mi zata ce masa ba, har ta gaji da zaman ta tashi ta koma dakinta ta shiga bathroom tai alwala ta gabatar da sallah isha'i, bayan ta gama ta hau saman gadon ta zauna, ta san ba zai shigo dakinta ba tun da yana fushi da ita, kuma idan taje can ba kula zai yi ba. A saman gadon tai ta juyi bachi ya ki daukarta, sauka tai daga saman gadon ta nufi dakinsa tana hawaye ta tura kofar ta shiga sai ta hango shi saman gado kwance. Bayansa ta kwanta ya kai hannu ta taba kansa. “Dan Allah ka yi hakuri ba zan sake ba” Shiru be ce mata komai ba, ta sake fada be ce komai ba ko matsawa be yi ba sai da kwanta bayansa tana kuka, sannan ya tashi zaune ita ta tashi zaune tana kallonsa. “Matsalar da ke tsakaninmu wacce za mu iya solving sai ace sai kin dauka kin kai gidanku? Idan ma zan kara aurene kina tunanin yin haka zai saka na fasa? Duk abubuwan da nake miki Rahma saboda ina son ki ne, kuma ina taka tsantsan da lafiyarki ne, ba wai dan ki juyani kamar dan ki ba” “I'm sorry” Ta fada da muryar kuka tana kama hannunsa, a sannan ya jimke hannunsa cikin nata alamar ya hakura kenan ya kai bakinsa ya sumbanci goshinta. “Wannan ya zama first and last, dan ba zan dauka ba” “Ba zan sake ba” Ta fada tana ta kallonsa, sai ya jata jikinsa ya rumgume suka kwanta tare. After like one hour ta dan dago kanta tana kallonsa ta ce. “Aliyu kana son haihuwa ko? Kana son yara right” “Yes” “Amman baka taba nuna min ba” “Saboda karki damu ne, kuma ga lalurar da kike fama da ita shiyasa ban damu da ki samu cikin ba” Hannu ta kai ta shafa fuskarsa. “Zan samu ciki zan saka ka farinciki In-Sha-Allah, zan haihuwa duk inda haihuwa ta kai sai na samo ta, zan kashe ko nawa ne na haihu Aliyu just for you” Murmushi yai ya sake sumbantarta. “Allah ya bamu mai albarka” “Amin” Ta fada tana kara kankameshi. “Amman ina son mu koma Abuja, hankali zai fi kwanciya idan muna can” “Yaushe kike son mu koma?” “Jibi” “To ki fara shiri daga yanzu” “Thank you, i love you” “I love you too” Lumshe ido tana sauraren sakwannin da yake aika mata masu zafi. ATAA POV. A lokacin da na shiga Bathroom din sai da nai fitsari a bandaki sannan na wanke shi, na fito na gyara bedroom din na fesa turare kamar yadda aka fada min, haka na bi duka dakunan na gyara ko wannen sannan na sauko da kayan mopping din na nufi inda na daukosu na aje. “Ke je ki cire Hijab din nan karna sake ganinki da shi sai idan fita za ayi, a cikin gidan ki yi ta saka mana Hijab kina watsa mana kora” Mama Fulani ta fada tana kallon cike da kyama daga can saman dinning da take zaune ita da yaranta suna karyawa, ba musu na nufi garejin na cire hijab dina na saka dankwali a kaina wanda hakan ya bayyana gashin kaina da na yi masa tsoro daya ya sauko har gurin mazaunaina. Da na tashi ban dawo part din Mama Fulani ba sai na wuce part din Ammy da alama ita ce da girkin tsakanin jiya da yau, domin ban same ta a falonta ba sai Anty Zee tace min Ammy tana part din Abbah amman ga abincin nan ta aje min, farfesun kaza ne a wani karamin plate sai wainar kwai da dankwalin turawa a plate daya da kuma katon burodi, da tea a wani babban kofi, duka an hade su a tray daya. Daukar tray nai zan fita sai Anty Batulu da ke murzawa fuskarta wani farin mai mai kamar sabulu ta ce. “Ina za ki je?” “Waje zan je na zauna na ci?” “Zauna a nan ki ci?” “Ammy ba zatai fada ba idan na ci a nan? ” Sai duk suka saka min dariya. “Hala Mama Fulani ta miki fada da kika zauna a falonta?” Anty Zee ta tambaya sai nai kasa da kaina ban ce komai ba. “Ammy ba ruwanta, idan ma muka saba sai ta fi son ki da mu,ba kamar wacan bakar matar ta ke ba” Anty Zee ta fada sai Anty Batulu ta kalleta. “Anty Zainab Ammy ta ce ki daina cewa haka” “Ke na fada tashi kije ki Fadawa Ammy ki ce na ce Mama Fulani mai bakin hali, munafuka kawai” Tana fadar hakan ta tashi ta nufi upstairs tana jan tsaki. jin hakan yasa na zauna a kasa na soma cin abincin hankalina a kwance har na ci na koshi, rabon da na ci abinci da naman kazan tun asibiti lokacin da Doc yake siya mana na restaurant, duk sai na ji babu dadi ina ma ace Nana na kusa da ni da na bata naman ta ci, sam bana son na ci wani abu mai dadi ba tare da Nana ba, hakan yasa na yanke shawara na shanya naman idan ya bushe sai na tarawa Nana idan naje sai na sake dafa mata shi ta ci. “Anty Batulu zan iya shayawa idan na koshi” “Eh to sai idan Garden za ki shanya shi, inda kowa ba zai gani ba” Tana bani amsar na tashi tare da ragowar naman na koma gareji na dauko wani dankwalina na nufi garden din na shimfida daga inda rana take haskawa na baza naman sannan na dawo part din na gyara ko'ina kamar yadda nai a part din Mama Fulani. Bayan na gama gyaran Ammy ta shigo part din jin kamshi na tashi yasa ta murmushi tana ta yaba min. “Kai haka na ke son yarinya da kuzari kazar kazar da ke, ai to za mu shirya kuwa idan kina son aiki ba kamar yaran gidan nan ba, manya da su amman sai dai a gyara suna zaune” “Ai daman Anty Zainab ta fada cewar nan da kwana biyu sai kin fi son ta da mu” Anty Batulu ta fada tana dariya, ni ma nai murmushi sai Ammy ta nufi upstairs tana fadin. “Eh mana to me ake da mu” Bata dauki lokaci ba ta fito rike da tufafi kusan kala biyar ta miko min. “Ungo idan kin yi wanka sai ki canja naga jikinki sun dan tsufa” Cikin wata irin murna da jindadi na saka hannu biyu na karbi tufafin ina godiya. “Allah ya saka da alheri na gode sosai” “Ba komai” Cike da jindadi na nufi garejin dan ajewa, kasa hakuri nai har sai na yi wanka na saka sai na soma gwadawa ina ta jujjuyawa rabon da wani yai min kyautar tufafi har na manta, kana ganinsu ka san masu tsada ne, na san ba zai wuce na Inteesar ba, domin ita ce kamar ni ganin yadda tufafin suka min cif kamar daman can nawa ne. Sam na manta da zancen gyarawa Ya Muhseen part dinsa har sai da na koma Part din Mama Fulani sai ta rufe ni da fada tana ta zagina kamar wacce bata san inda na fito ba. “Gidan uban wa kika je kika zauna? Ba na ce ki je ki gyarawa Muhseen part dinsa ba? Shine dan kin maida ni shashasha kika tafiyarki ko? Zo nan” A tsawa ce take min fada kamin ta ce na zo, ni kuma duk tsoro ya kamani jikina nata rawa kamar nazari idona har ya fara hawaye, domin na fahimcin kiran da take min dukana za tai. “Aa ni nace ta bari sai gobe” Ya Muhseen ya fada yana kashe min ido daya, kasancewar duka yan 'uwansa basa nan daga ita sai shi ne a dinning din. “Ko?” Sai na gyada kai. “Eh haka ne, shi yace na bari sai gobe” “Yaushe ka ce mata haka?” “Dazu, dauki ga abincin ki can” Ya karasa yana nuna min kasa kusa da Mama Fulani. Sai na kasa zuwa na dauka ina ta jin tsoro shi kanshi ya lura da hakan. “Mama gaskiya tsoron ki take” “Tsorona dodo ce ni?” Ta daka min tsawa. Sai na amsa mata da sauri ina girgiza kai. “Aa” Ya Muhseen ya tashi ya nufi inda abincin yake ya dauko ya miko min yana dariya tare da fadin. “Ko ni da kika haifa a tsoronki na ke balle kuma ita” “Aa ni ban haife ka ba, dana ya can sokoto Aliyu dan albarka” Mama Fulani ta fada tana mikewa tsaye daga dinning din. Sai Ya Muhseen ya saka dariya “Kowa ya ganshi ai yaga danki halinku daya Mama, har ya fiki rashin tausayi” “Kanka ake ji” Ta fada tana tabe baki sannan ta nufi kitchen, shi kuma ya miko min abinci ina karba tana fitowa daga kitchen din tana fadin “Idan kin ci abinci ki aje wannan plate din da cup din a gurinki, da shi za a rika saka miki abinci” “To” Sannan na juya na fita, tea a cup din sai wainar kwai da dankalin turawa a plate din da burado kadan, ban ci komai ba kasancewar na riga na ci na bangaren Ammy na koshi, sai kawai na aje a garejin na kwanta a saman tabarma ina ta tunanin Nana, ko a wane hali take yanzu oho, gashi ba ni da waya balle na kira ta ji muryarta. After like one hour har bachi ya fara daukata na ji an taba garajen ina dagowa sai na ga Ya Muhseen cikin shiga ta kananan kaya ya dora rigar likitoci a sama, kayan sun karbe shi sosai ga fuskarsa da far'a yana aiko min da murmushi, ni ma murmushin nai masa kadan na tashi zaune. “Zo ki bude min gate” “Ba akwai mai gadi ba?” “Ke nake son ki bude min” Na tashi kamar yadda ya bukata ina gyara daurin dankwalina na fito daga garejin na nufi gate din, sai da na wuce gate biyu sannan na iso a babban gate din nai ma mai gadin magana ya nuna min yadda ake budewa na bude sannan na hango shi ya taso motar ya nufo inda nake tsaye da gudu kamar mai shirin kade ni, ni ko na ratse gefe na rufe ido ina jiran ya kade ni sai kawai na ji ya saka min ya jefeni da chocolate. Murmushi nai na duka na dauki chocolate din ina kallonsa. “Sarkin tsoro, daman saboda na gwadaki nai kuma na ga gashin nan na ki” Ya fada sannan yai gaba abunsa, ni da mai gadin muka bi shi da kallon mamaki, ni dai ina jin son barkwancinsa da yadda yake da son wasa da ni. Mai gadin ya riko dayan gate din ni kuma na riko dayan za mu rufe na ji an ce. “Ke” Juyowa nai sai na hango wani fari saraurayi tsaye jikin wani katon gate da ke facing din na su Mama Fulani yana sanye da uniform din sojoji. Ba musu na saki gate din na nufi inda yake tsaye cikin mugun tsoro domin Allah ya zuba min tsoron soja fiye da dan sanda. “Ina wuni” “Ina kwana dai” Ya gyara min yana murmushi. “A can gidan kike?” “Eh" “Gurin wa kika so?” “Aiki na ke a gidan” “Aiki?” Ya maimaita, yana kallona kasa da sama. “Wa kike yi ma aiki? Mama Fulani ko Ammy?” “Dukansu” Na amsa muryata na gargada. “Ki daina jin tsoro ba wani abun zan miki ba. Ya sunanki?” “Aisha” “Ashe mamana ce ke, kina da kyau Aisha ke fulani ce?” “Aa buzuwa ce” “Shiyasa kike da kyau sosai ga gashi, an taba fada miki kina da kyau?” Na shiru ina yin kasa da kaina sai yai dariya. “Kar ki ce ban saba ganin kyawawa ba, na saba ganinsu ni ma ai kin ga na fiki kyau ko?” Na dan dago na kalleshi sai ya shafa kansa yana dariya. “Sunana Kamal Isma'il Isa, nan ne gidan mu kuma ni soja ne, idan kikai wani abu sai na kama ki, dan haka ki yi hankali” Ya fada yana fiddo yar karamar bindigasa ya nuna ni da ita, aiko ba shiri na ranta cikin na kare cikin wani irin gudu da ban taba sanin ina da shi ba na zarce cikin gida, ina waigensa ya biyoni yana ta dariya. *Littafin nan na kudi ne* *Z A K I -it's not free, pay 300 to 0314795884 Abubakar Gt bank, then send the evidence via 08036126660* 19. Nasir ya fada masa a unguwar da ak fada masa ya sa an bincika amman ko fulani ba a samu a unguwarba balle wasu buzaye, zancen wani ja gini duk karya ce. Jin wannan yasa Aliyu ya zabi ya cire nemanta da kokari fahimtar da ita idan ya ganta a ransa, tun da be san inda take ba, and gashi garin nemata har suna kokari mom samun matsala da Rahma, and idan ma yace dole sai ya nemota ya ai wani sabon aikine a gareshi, but he know one thing for sure tunanin zalincin da akai ma yarinyar nan ba zai taba fita a zuciyarsa ba, kyauta kuma ba zai taba gushewa a idonsa ba. He keep himself busy these days saboda shirye shiryen da suke na zuwa Abuja ya san akwai aikin kamfaninsa yana jiransa, kamar yadda ya saba and Rahma ta masa complain cewar tana on ganin likita idan sun koma Abuja saboda matsalar haihuwarta. Da kanshi ya dauke ta suka je sukai Momynsa da Daddynsa sallama sannan naje gidansu Rahma suma sukai musu bankwana, domin tafiyarsu gobe ne. Farinciki gurin Rahma ba a magana tana ganin da zarar sun koma Abuja komai na damuwarta ya wuce, sun bar garin da Ataa take hakan zai saka hankalinta ya kwanta gashi kuma ta jin cewar idan ta je ga babban Likita kamar Doc Perry matsalar haihuwarta zata gushe, duk da acan din ma tana fargabar Mama Fulani saboda zancen haihuwa da take mata gashi kamar bata san Allah ne yake komai ba. ATAA POV. Ina ta gudu yana biye da ni a baya har na nufi garejin na boya sai kuma na wuce falon Mama Fulani a tunani ba zai iya biyo ni ya shigo ba, amman ga mamaki na sai ya biyoni har cikin Falon, mamaki ya hana ni cewa komai sai bin sada nai da iso, shi kuma yana ta murmushi kamar daman can mun saba irin wannan wasan da shi, zaunawa yai saman sofa yana maida bindigarsa aljihu. “Ba ruwana idan suka zo suka maka fada” “Ba za su min ba, sai dai ke su yi miki ke da kika kawo ni” Ban sake wata maganar ba, gabana sai faduwa yake gudun kar Mama Fulani ta fito ta ganshi, gashi ban san mi zan ce mata ba, ban gama tunanin abunda zan yi ba sai ga Mama Fulani ta fito daga dakinta sanye da doguwar riga da alama wanka tai ta canja tufafi. A take hantar cikina ta kada tsoro duk ya bi ya cika min ciki, tana sauko ya mike tsaye a mamakina sai ganin nai ta sakar masa fuska tana masa murmushi. “Kamal ne?” “Ni ne Mama ya gida?” “To ba dai Aliyu ya zo ba balle na ce, na san sai idan yana nan kake shigowa gidan nan” Murmushi yai ya shafa kansa. “Kawai dai yau na ce bari na zo na gaishe ki” “Ato ka kyauta gaskiya, ka yi abun kai, ina Hajiya Uwani?” “Tana nan lafiya kalau” “Ke shiga kitchen ki dauko masa cup ki bude freezer ki dauko masa lemu” Mama Fulani ta fada min, sai na juya da sauri na nufi kitchen din, ina shiga na duba inda kofuna suke na dauko tare da lemun na dawo falon na kawo a gabansa na dire. “Mama ina kuka samu wannan mai aikin?” “Wallahi wata wacce ta saba kawo mana mai aiki ta kawo ta mana ita” “Okay ni kan na ce ban san da zamanta a gidan nan ba” “Bata dade da zuwa ba” “Okay” Ya fada yana mikewa tsaye ba tare daya sha lemun ba yai mata sallama ya fice yana ta kallona kamar zai yi magana sai kuma be ce komai ba har ya fice. “Zo ki dauki kayan nan ki maida su kitchen” Mama Fulani ta fada tana daure fuska. Kamar daman umarni na ke jira sai na nufi lemun na dauka na kai kitchen na aje sannan na fito na dawo falon na zauna inda na sabawa kaina da zama na kurawa tv ido. Misalin sha biyu na rana da yan mintuna Mama fulani ta fito ta shiga kitchen ta dora abincin rana, guraren karfe biyu ta kammala abincin sannan ta fada min na dauko plate dina ta zuba min abinci a ciki, sai na tashi da sauri na nufi garejin na dauko abincin safe da ban ci ba na nufi garden na siyayarda tea Wainar kuma na cinye, daman ni ba soyayiyar dankali bane dan haka na shanya shi a inda na sanya ragowar kazar nan ta dazun. Sannan na kunna fanfo na wanke plate din na dawo part dinta na kawo mata. “Aje kasa” Sai na risina na aje da alama kyamata take da har ba zata iya rika plate din ba, debo abincin tai ta zuba min a plate sannan ta zuba min miyar bata saka min naman da ke miyar ba ta ce na dauka, ni kuma na dauka da sauri na fito balcony na zauna ina cin abincin a hankali. Ina daf da cinyewa Ya Muhseen ya shigo gidan da motarsa, inda manyan motoci suke yai parking sannan ya bude motar ya fito yana matsa remote din motar tana kara. “Pretty nan kike cin abinci?” “Eh sannu da zuwa” “Yauwa” Ya fada sannan ya shiga part din Mama Fulani be dade ba ya fito ya nufi wani bangare na gidan inda nake saka ran a can dakinsa yake, sai da na gama cin abincin na je na wanke plate din na maida shi gareji na aje sai na kwanta a gurin, ina ta tunanin yadda zan iya da zaman gidan, anya zan iya juye wulakanci irin na Mama Fulani? Amman ya zan yi tun da na riga na zo, Sai da la'asar na fito daga garejin nai alwala na koma nai sallah sai na nufi part din Ammy, tambayar ta nake son yi domin ita ce mai far'a da son mutane ba kamar Mama Fulani ba. Da sallama na shiga sai ta amsa min tana zaune kasa tana cin abincin. “Tun dazu na ke nemanki ba ki shigo ba” “Je kitchen ki dauko tuwon ki ga shi can kina cin tuwo da rana dai ko?” “Eh ina ci” Na gyada mata kai sannan na nufi kitchen din, sai na samu tuwon shimkafa da miyar yauki a rufe cikin wani plate an saka min har da man shanu, ga wasu manyan tsokoki a sama. Daukowa nai na fito sai na koma can kusa da kofar shigowa falon na zauna na soma ci, ba wani da yawa zan bi ba ni kaina na san cikina ya cika da shimkafar da Mama Fulani ta bani amman ina son tuwo sosai ga kuma manshanun da aka saka a sama da namomi ba zan iya barinsu ba. Ina cikin cin abincin wayar Ammy tai kara alamar kiranta akai, picking tai ta kara a kunne ban san mi aka ce mata ba na ji dai ta yi amsa da okay, sannan ta kalleni. “Mamana kin iya zuba tuwo?” “Eh na iya” “To shiga kitchen ki samu plate ki bude fula gata can dinning ki zubawa Muhseen ki rufe sai kije ki kai masa kin ji” Sude hannun na yi na tashi na nufi kitchen da kuzarina na dauko plate din sannan na dawo dinning na zuba nasa miya a wani plate din sannan na saka tuwon a dayan plate din na rufe na dauka na nufi part din Mama Fulani, Ya Muhseen kadai na samu a falon yana shan kankana da fork, ganina yasa shi murmushi ya mika hannu biyu ya karbi abincin. “Yauwa thank you, ke kin ci abincin ki?” “Shi na ke ci ka karani” “To dauko ki zo nan ki karasa” “Zan fi jindadi ci a can” “Saboda Mama tana miki fada a nan ko?” Ya fada yana bude tuwon. “Kin ga kin fini cin abinci yanzu na ganki kina cin shimkafa yanzu kuma kina cin tuwo” Murmushi nai har na soma jin kunya na baibayeni. “Dauko min ruwa” Na nufi kitchen din an bude freezer na dauko gorar ruwa da cup na kawo masa. Kamar daga sama na ji muryar Mama Fulani tana masa fada. “Wai Muhseen baka kyamar yarinyar nan ne? Ka cika shige mata fa bana sin haka” “Miye a jikinta?” Banza tai masa tana jin haushin tambayar da yai mata, sai gyara tsayuwar jikar da ke hannunta take da alama fita za tai. Ni dai ban ce komai ba ina tsaye ina jin umarninsa ko zai sake bukatar wani abun ne, ban ji ya ce komai ba hakan yasa na fice na barsu ita da danta na koma part din Ammy. Da sallama na shiga kamar dazun, wannan karon kishingide na sameta tana kallo tv. “Mamana amman ku fulani ne ko?” Ta fada tana kallona. “Aa ni buzuwa ce” “Wane gari kike?” “Sokoto” “Tare da iyayenki kike zaune?” “Babana ya rasu mama ce kawai” “Allah sarki, ita ta turo ki aiki a nan kenan? Ina kika san Maman Salma ko yar'uwarku ce?” “Aa ba mu da alaka da ita zaman unguwa ne kawai” “Allah sarki, amman kina da kanen ko? Ke ce ta nawa gidanku?” “Ni ce ta farko ina da kane amman ya rasu” “Ayyah Allah ya jikanshi” “Amin” Daga nan bata sake magana ba har na gama cin abincin na tashi na maida plate din na wanke hannuna na dawo na zauna. Gefen kujerar muka cigaba da kallon a tare, sai ga Ya Muhseen ya shigo rike da plates bakinsa kunshe da nama ya miko min plates din. “Kai kitchen” Na karba da hannu biyu na nufi kitchen din na aje. Ban san abunda ya fadawa Ammy ba kallona kawai take tana dariya. Kamar yadda shi ma yake dariyar har na soma tsaguwa, ma tashi na bar musu falon na dawo gareji na zauna ina turo baki kamar an min wani abu. Tun da na dawo ban koma fita ba sai da magariba, shi ma sai da na sauke farilla sannan na fito harabar gidan na zauna ina ta kallon fitilun da suka haska gidan gwanin sha'awa. Ban tashi daga gurin ba sai da aka kira isha'i sannan na nufi garden da tsoro nai alwala na dawo garejin nai sallah ta sai na kwanta a gurin ina ta jin tsoron da ban san ta ina yake fito min ba, kamar jiya ba ni kadai na kwana ba, yau kan tsoro ya kamani sosai ko iska ya kada sai na ji kamar wani aljanine zai kama ni, da naji na kasa natsuwa da gurin ne na taso na koma Part din Ammy na zauna, ina ta kallon Anty Zee Inteesar da ke cin abinci a plate daya. “Shiga kitchen ki dauko na ki” Inteesar da fada min, ni kuma na tashi na shiga kitchen din a inda na samu abincin dazu nan aka sake aje min wani yanzu ma tuwo ne kamar dazun sai dai wannan miyar ganye ce ba kamar dazunda taie miyar yauki ba. Dauko abincin nai na fito waje falon na zauna na ci sai da na koshi sannan na tashi na maida plate din na wanke hannuna. Haka rayuwata ta cigaba da tafiya a gidan kullum Mama Fulani da Yayanta cikin nuna min kyama suke, a gurin Ya Muhseen kawai na ke samun sakewa har dadi nake ji idan yana nan, tun ina kin sakewa da shi har na soma sakewa kwanan biyu da nai a gidan sai na ji kamar daman can na basa da gidan, sai na fara sabawa da halin Mama Fulani da kuma Ammy da bata nuna min kyama, sai dai abu daya ke damuna kwana a gareji da kuma wanka idan zan yi sai naje garden na boya a bayan itace sannan nai wanka, da sabulun da Ammy ta ba ni, idan kuma ba haya zan yi sai dai na raba a dakin mai gadin na shiga nai. Yau ma na yi aikina kamar yadda na saba, bayan na gama da bangaren Mama Fulani na je sashen Ammy nai mata nata sannan na shiga bangaren Ya Muhseen shi ma na gyara masa nasan dakin da falon na goge komai kamar yadda na fara yi masa a jiya na fito na dawo bangaren Mama Fulani, kowa na falon kasancewar Weekend ne Ya Muhseen da Anty Maryam na zaune a kujera daya tana nunawa Ya Muhseen wani abu a wayarta, Mama Fulani kuma na zaune kasa tana mulka fulawa, sama sama nake jin tana firar dan ta nan tafe dole ta dafa masa abunda ya ke so, sai da ta gama mulka fulawar sannan ta kalleni. “Ke je kitchen ki yanka min kabeji, yana nan a roba” Na amsa da to ina mikewa tsaye na nufi kitchen din, yana jiyo lokacin da Ya Muhseen ke fadar cewar ina da gashi, har Mama fulani na masa fada wai yana ta abu kamar be tana ganin kyakkyawar mace ba. Karamar kujera na samu na zauna na dauko daya daga cikin wukaken da suke hade guri daya na soma yanka kabejin, ban ankara ba na yanke kaina sai jini, ban san lokacin da na kwala wani uban ihu ba na mike tsaye da sauri jikina nata rawa abun ka da mao tsoro ga shi ban saba da amfani da wuka sosai ba, rabon da naji ciwo har jini ya fito haka har na manta. Cikin sauri Ya Muhseen ya shigo kitchen din. “Daman na san yankewa kikai” Ya fada yana kallon yadda jinin ya samu hanya sai bulbulowa yake, ni ko ina ta kuka kamar hannun ya cire gaba daya, wanda hakan yasa Anty Maryam shigowa kitchen din tana tambayar ba'asi. Wani dogon tsaki taja ganin ganin a yatsa ne kawai na yanke amman nake wannan ihun. Hannun nawa Ya Muhseen ya riko muka fito daga kitchen din ina ta kuka sosai muka nufi kofar fita jinin nata zuba. Bangarensa yaje da ni ya dauko wani dan karamin akwati ya bude ya saka ruwan nan masu shegen zafi ya goge min gurin ya saka min wani maganin sannan ya saka min kada ya rufe min yatsan. “Sarkin raki” Ya fada yana kallon yadda hawaye suka bata min fuska, na turo baki waje kamar yadda yara suke idan sun ji ciwo. “Kadan ne fa kika ji ciwon amman kin cika mana gida da ihu ke sagartacciya ko?” Na yi kasa ta kaina ina kallon yadda yake aiko min da murmushi. “Shikenan zaki iya tafiya” Ina juyowa shi ma ya tashi tsaye muka fito tare, ina gaba yana bayana har muka shiga part din Mama Fulani. “Muhseen karka sake shiga safgar yarinyar nan” “Mi akai?” “Na dai fada maka? Ba ita ba kai daga yau, ke kuma dauko Mopper ki goge jinin nan” Ta karasa tana kallona, sai na nufi inda mopper take na dauko na goge duk inda jinin ya diga sannan na koma kitchen din, zan cigaba da yanka Anty Maryam ta shigo wai na zubar da wannan kabejin basa son sa na yanka wani sabo. A kwandon shara na zuba kabejin na dauko wani a freezer dake kwance na soma yankawa, a hankali nake har na gama sannan na aje mata shi na fito na nufi part din Ammy. A lokacin da na shiga falon ita kuma tana kitchen tana hada fruits salad, a falon nai zamana har aka yi azahar sannan ta fito ta miko min plate da spoon. “Ga abincin ki” Hannu biyu na saka na karba ina mata godiya. A gurin na zauna na ci sannan na aje mata plate din a kitchen, na fito na nufi garden na wanke hannuna da fanfan gurin, nai zamana gurin ina ta kallo wasu kananna tsuntsaye dake cikin keji suna cin giďa, ina jin lokacin da motacin har biyu suka tsaya a habarar gidan amman ban tashi ba sai da na gaji da zaman na fito na ratsa motocin zan shiga part din Mama Fulani sai na soma jin kamshin wani turare mai dadi, da na taba ji sai dai ba zan iya tuna inda na ji shi ba. Tura kofar falon nai na shiga da sallamata babu wanda ya amsa min sai Ya Muhseen, Anty Maryam da Anty Rukaiya duk sun sha jinin jikinsu ko motsin kirki basa yi, Mama Fulani kuma na zaune a kujera daya da wani saurayi tana bare masa abaya ba tana mika masa, da na kalleshi da kyau sai na ga she mutumen da nai ma aiki kamin na dawo Abuja hakimce a kujera yana kallona da mugun mamaki. *Z A K I -it's not free, pay 300 to 0314795884 Abubakar Gt bank, then send the evidence via 08036126660* Idan ba ki biya ba karki karanta hakkin wani. Idan kuma kin ji zaki iya Bismillah. 20. Ba ni kadai yake kallo ba, gaba dayan jikina da duk wani motsi takun da nake na karasa gurin da na saba zama na zauna yake kallo. Nima idona na kansa ina ta mamakin abunda ya kawo shi gida, da alama yana da kyakkyawar alaka da mutanen gidan, domin yadda na ga Mama Fulani na bare ayaba tana bashi yana ci kamar wani karamin yaro ya nuna yana da muhimmanci sosai a gareta duk da ban san alakarsu ba. “Ke bana son kallo” Ya fada yana kallona, sai duk suka juyo suka kalli inda na ke kokarin zama. “Haka ta ke da shegen kallo kamar yar kauye” Anty Maryam ta fada tana watsa min harara. Ya Muhseen yaja tsaki. “Aliyu kana da matsala Wallahi, taya akai kai kaga tana kallon ka? Haka kawai za ka ce kar ta kalleka kai kuma ka kalleta?” “How dare you zaka fada min wannan maganar sa'an ka ne ni?” Aliyun ya fada yana mikewa tsaye cikin zafin rai kamar zai da ki Ya Muhseen. Ya Muhseen ya mike tsaye yana kara jan tsakin. “Rayuwarku batai ba Wallahi, arziki ai ba hauka ba ne, shikenan dan tana talaka bata da gata kallon ma sai an shar'anta mata kalar da za tai?” “Muhseen enough! Wai Aliyu ba yayanka ba ne kake fada masa wannan maganar?” Mama Fulani ta fada tana mikewa tsaye tare da shiga tsakaninsu. “Shikenan dan ya girmeni yayi ba daidai ba ba za ayi magana ba? Waye shi?” “Amman ka san Aliyu ba ita ya hana kallonsa ba, ko su Maryam da Batulu da suke kannensa basa tsare shi da ido ko? Ina ruwanka da shi ne? Wai ku kullum kuka hadu a waje daya sai fada ya shiga tsakaninku? Kamar kare da Mage! Haba sai ka ce wasu abokan adawa” Mama Fulani ta fada cikin yanayin da ke nuna damuwarta karara. Ya Muhseen be sake cewa komai ba ya watsawa Aliyu harara ya fice daga falon, sai da ya fice sannan Aliyu ya koma ya zauna sai ya maida idonsa a kaina, ni dai nai kasa da idona gudun kar Mama Fulani ta ce na yi laifi, amman idan ta shi ne bana tsoron duk abunda zai fada, lokaci zuwa lokaci idan na dago na sai na ga ni yake kallo, ka ji wani tsantsar zalinci amman ni ya ce ba zan kalleshi ba. A dago ta hudu da nai muka hada na watsa masa harara kadan sannan na maida idona kasa. “Ke tashi ki fita bakar munafuka” Mama Fulani ta fada min a tsawace tana watsa min harara, ba musu na tashi na fice daga falon, na koma garejen na zauna abuna ina ta jin zafin kalmar munafuka da Mama Fulani ta kira ni da ita. Zaune nai a gurin na rumgume hannayena ina turo baki kamar an min wani abun bayan wannan, ina jin motsin shigowar Ya Muhseen a garejin nai saurin gyara zamana. “Pretty ta so muje part din Ammy” Ya fada yana zuba duka hannayensa aljihu, ni kuma na mike tsaye na karasa inda yake ba tare da na san bakina yana nan a yadda na turo shi ba. “Fushin ne har yanzu? Ki daina damuwa da lamarin Mama haka rayuwarta take, amman Aliyu idan yai miki ki rama” “Idan na rama ai Mama Fulani fada za ta min, ko kuma shi ya dake ni” “Ba zai dake ki ba, wai baya dukan mata sai maza, Aliyu ba shi da kirki ko kadan” Ban sake cewa komai ba muka jero ni da shi muna tafiya har muka isa part din Ammy, Anty Humaira ce zaune ita da Inteesar suna playing wani gate da ke cikin plate da wani abu mulmulalle, kusa da Anty Humaira Ya Muhseen ya zauna ni kuma na zauna daga can gurin kofar shigowa falon ina kallonsu, Anty Humaira aka fara ci kamin aci Ya Muhseen abun gwanin sha'awa sai dariya na ke. “Zo mu yi” Ya Muhseen ya fada min yana kirana da hannu, sai dan bata lokaci ina jiran naji ko wata daga cikinsu zata ce ba za tai da ni ba, da ban ji komai ba na taso na karaso kusa da Inteesar na zauna aka so ma yi da ni, duk da ban iya komai ba amman Ya Muhseen ne ke fada min inda zan dora abun sai dai hakan be hana a ci ni ba, Inteesar ce kawai wance ba a ci ba sai dai ta ci wani. “Yanzu kan a dora kudi idan an ci zan bada dan kunne na” Inteesar ta fada tana aje dankunnen zinarin da ke kunnenta. Sai Ya Muhseen ya cire agogon hannunsa ya aje. “Ni ma ga agogo na” Anty Humaira kuma ta aje karamar wayarta. “Ni ma na waya” “Ke mi za ki saka?” Sai nai shiru ina kallon Inteesar da tai min tambayar kuma ta tsare ni da ido tana kallona. “Ita bulala biyar biyar za a mata idan an cita” Ya Muhseen ya fada yana dariya nima dariyar nai na ce. “Ban yarda ba, gaskiya ba ban yarda ba, idan an ci ni a saka ni aiki kawai” “Wanki za ki min” Inteesar ta fada Sai Humaira ta sa dariya tana fadin. “Inteesar ke muguwa ce Wallahi” Har Inteesar ta bude ba ki za tai magana sai na ga ta mike tsaye da sauri da kamar razana a fuskarta. “Ya Aliyu” Humaira ta kalli kofar da sauri sannan ta gyara zamanta, ni kan kallo daya nai masa na dauke kaina har ya karaso cikin falon ya zauna. “Ya Aliyu sannu da zuwa” Inteesar ta fada tana nufar inda yake ta zauna, sai ya mika hannu ya kama hannunta. “Yauwa Intee, ina Ammy?” “Tana dakinta” A nan Humaira ta mika masa gaisuwarta sai yai banza da ita be ko kalli inda take ba, ya mike tsaye ya nufi bedroom dinsa Ammy yana rike da hannun Inteesar. “To mi nai kuma? Na gaishe shi ya ki amsa min” Anty Humaira ta fada tana kallon Ya Muhseen. “Wacan dan iska kike damuwa da shi kamar ba ki san halinsa ba” Ya Muhseen ya fada yana tashi daga kasan da yake zaune ya koma kusa da ni saman cushion ya zauna, a nan Anty Humaira ta mike tsaye ta nufi daya daga cikin dakunnan da suke gefen na Ammy. Ni kuma na taso na baro part din na nufi garden kusa da fanfo na zauna na kunna fanfon na tara kafafuna ina ta wankewa ina wasa da ruwan. Kamshin turaren da na ji ne yasa ni saurin juyowa sai ganinshi nai tsaye nesa da ni yana ta kallona da alama wata maganar yake son min ya kasa ko kuma so yake ya ce na kalleshi oho. Juyowa nai na cigaba da abunda na ke, sai jin kamshin turaren nai ya karu hakan ya tabbatar min kara matsowa yai kusa da ni. “Ina Mahaifiyarki? Tana raye?” Kamar saukar aradu haka na ji tambayarsa ta sauka a kaina ta shiga kunnena. Juyowa nai na mike tsaye na daga kaina ina kallonsa domin ya Ya Muhseen tsayi da dan fadi, balle kuma ni da ba wani tsawo ne da ni sosai ba. “Idan tana raye kasheta za kai? Saboda asirinku ya rufu ko? Karka da mu ba sai ya sake zalintar mu ba, babu wanda zai sake jin wannan sirrin, ba zan fadawa kowa ba, sai dai akwai ranar da komai baya boyuwa ko da na yi kokarin yin hakan” Na fada masa sannan na ratsa gefensa ban wuce sai ya juyo fuska a hade ya ce. “Ba ni na saka aka cire mata koda ba, biyansa nai” Juyowa nai na kalleshi. “Shi haka ya fada lokacin da na kai shi gurin yan sanda, sai ya juyar da abun a kaina aka kulleni a cell har na tsawon kwana hudu, ya bar ni da wahala babu wani abun da za ku fada min da zai saka na yarda da ku, cuta kun riga kun cuce ni kuma babu abunda zan yi iya yi a kai, kun cire kodar mahaifiyata kun raya wata, sanadin cire kodar da kukai na rasa kanena, aikin da na ke a nan saboda ita nake yi saboda na samu lafiya, na rufa min asiri ka taimake ni karka saka nai abunda zai saka Mama Fulani ta koreni a gidan nan, zalinci ne kun riga kun min, kuma na maka alkawarin ba zan fadawa ko na gidan nan ba, ba zan tona maka asiri ba, domin tona maka asiri daidai yake da bakin aikina a gidan nan, idan kuma na bar nan ban san ya rayuwata zata kasance ba” Na karasa hawaye na bin fuskata. Sannan na juya na fice daga garden din hawaye na bin fuskata, garejen na nufa na zauna ina ta kukan bakinciki a da mutanen nan suka saka min, hakika sun zalince ni iyakar zalince abunda ba zan iya yafewa har duniya ta nade. Da zaman ya isheni ne na tashi na fito harabar gidan na nufi gurin gate na fice na farkon na wuce na biyu na isa na uku na bude na fita sai na ji wani iska mai dadi yana ratsani, daman garin hadari ya hadu sosai kamar za a sako da ruwa, iska sai kadawa yake a ko'ina, rumgume hannayena nai ina ta kallon titin da ba kasafai mota take wucewa ba ga manyan gine gine gwanin sha'awa komai a tsare, gaskiya garin Abuja yana da kyau sosai. Ina tafiya ina jin takun mutum a bayana sai dai hakan be sa na waiga ba har sai da na ji an gashin kaina, saurin juyowa nai sai mukai ido hudu da Kamal yana sanye da shadda sky blue fuskarsa dauke da murmushi. Ban san hawaye ne a fuskata ba har sai da ya nuna fuskar tawa yana tambaya. “Mi yasa kike kuka?” Hannu na kai na taba sai na ji hawaye a fuskata sharewa nai sai wasu suka zubo min. “Miyasa kike kuka? Ko kin marmarin gida ne?” Ban ce masa komai ba na daga kaina a sama ina ta kallon hadari, kokari na ke naga na tsayar da hawayen amman suka ki tsaya min. “Yi magana mana ko cikin gidan ne akai miki wani abu?” “I zuwa yanzu nima ban san dalilin kukana ba, gida na ke so ko wani abun yake damuna ban sani ba” Na fada ina fashewa da kuka, kuka nake yi sosai irin kukan nan da ke fitowa mutum da ko ina, wanda ban san dalilinsa a yanzu ba. Sai ya ciro handkerchief dinsa ya miko min. “Share hawayenki fada min abunda akai miki” “Kai ba ka kyamar talaka?” “Wani ya nuna miki kyama ne?” Na yi shiru ban ce komai ba sai kallon kyalen na ke. Sai ya dago fuskata ya saka kyalen ya share min hawayena. “Ni ma lokacin da ina kamar na yi irin wannan kukan, ina ta tunanin makomata da ta mahaifiyarta da ta kanena, zan mu jidadi ko aa” Na kauce fuskata daga rikon da yai min, sai ya cigaba da maganar ba tare da ya damu ba. “Na san darajar talaka, su ne mutanen da na kaiwa kuka aka taimake ne a lokacin da nake bukatar taimako,ba dan talakawan ba, da yanzu ban samu wannan aikin ba, ban kai wannan matsayin ba” “Amman mutane da yawa basa son talaka, suna nuna mana kyama kamar mu din wata al'umma ce ta dabam” “Kar hakan ya dame ki, yatsun hannunki ma ba ayi su daidai ba, taya kike tunanin mutane ma za su yi daidai a tunani da hankali? Arziki da taluci duka na Allah ne, a lokacin da na ke kamar ki talaka ne mai neman na kansa, amman yanzu gashi ina cikin masu kudin suna yi da ni” “Ba arzikin ne damuwata ba, kyamar da ake nuna mana ne ke damuna kuma....” “Aisha” Kiran da Inteesar tai min yasa ban karasa fadar abunda zan fada ba, na juyo da sauri na nufo cikin gida a lokacin har an fara ruwa sai dai ba sosai ba. “Mama Fulani na kiranki” Jin hakan yasa na hada da gudu na dan na isa part dinta cikin sauri. Ina shiga ciki ta rufe ni da fada. “Dan ubanki ba aiki kika zo ba da zaki kama hanya ki fita” “Ba wani gurin na je ba, ina bakin gate ne...” Ban gama rufe baki ba ta wanka min kyakkyawan mari ban san lokacin da na fashe da kuka ba nai baya da sauri dafe da kuncin ina jin yadda yake min wani mugun zuji. “Mama dan Allah ki yi hakuri ba zan sake” “Ki ma sake ki ga yadda zan yi da ke a gidan nan, yar iskar yarinya kawai, uban wa kika sani a abuja da zaki kama haya ki fita, ko bakin yawon gantalin na ku ne ya yayan takawa za ki fara? Salon ki bace a dora mana lalurar neman ki ko? Jahilar banza, wuce ki ba ni guri” Da sauri na fito daga falon jikina na rawa ina ta kuka na nufi garejen da na ke kwana, wani abun mamaki sai na samu Aliyu a ciki tsaye kan tabarmata kamar mai jiran shigowata. ALIYU POV. Ji yai kamar ta saka gatari ta sare duk wani kuzari da karfi da yake jikinsa da zuciyarsa, hawayen da na ga suna zuba idonta a lokacin da take fada masa maganar da tafi ko wace zafi a duniyar nan yasa shi jin babu dadi. Azzalumi take kallonsa, then why ma zai mata magana daga ganinta? Taya zai fahimtar da ita? It's necessary for him? Zalincin da ya ke gudun da kira shi da shi ashe haka take kallonsa, sai ya ji ya damu da kukanta da kalmominta da kuma kallon da take masa na azzalumi. Kamar marar muzari haka ya fito daga garden din ya dawo part din Mama Fulani ya zauna. A lokacin tana kitchen tana hada masa fried rice saboda ta san yana sonta sosai. Zaman kawai yai amman be zuciyarsa tana waji gurin dabam tana yayo masa wani tunanin akan Ataa. Tashi yai ya shiga kitchen din yana fadin “Mama favorite dina kike dafawa i know” Sai ta juyo ta kalleshi tana dariya “Eh mana ai dole nai maka abunda kake so Aliyu, wai ina yarinyar nan ne ma ta yanka min albasa?” Yasan Ataa take nufi dan ko ba a fada masa ba yasan aiki ta zo yi a gidan, kuma ya san Mama Fulani ba zata saka yayanta aiki ba sai dai mai aiki. “Ina take zama hala? Waya kawo muku ita?” “Wannan matar ce mai kawo mana yan aiki, ita dai wannan ina ganin kamar ba za mu dade da ita ba, dan kazama ce kuma bata cika son aiki ba ga shegen shishigin tsiya, and i hate yadda Muhseen yake rawar kai a kanta” “Ina take?” “Gareji take kwana, ban san inda take ba balle ta gyara min albasar nan” Kofar baya ta kitchen din ya bude ya fita ta nan ya zagaya gurin motocin ya isa gareji, bude ya same shi garejin an shimfida tabarma a ciki sai yan jakarta a gefe rabe da plate da cup a gafe daya ta rufesu da dankwalinta mai raga. Yana kallom gurin zuciyarsa na sosu a tunaninsa kamar be dace ta zauna a nan, if he is one da yai causing duka wannan matsalar a rayuwarta. Jin kukanta ne yasa shi juyowa yana kallon kofar gajerin sai gata ta shigo tana dafe da fuskarta tana kuka. Yawun bakinsa ya hade saboda sautin kukanta da ke shigar masa har cikin gashi yana ta masa ruri a kunne kamar shine silar kukan. Tsaya yai kallonsa. “Bakin azzalumi mi kake nema a nan kuma?” Ta fada masa kai tsaye tana kallonsa da jajayen idonsa. Yana jinjina kokarinta yadda ta ke fada masa duk abunda ya zo bakinta, ba karamin burge shi take ba at least ya hadu da mai iya fada masa magana kai tsaye bayan iyayenshi. “Bayan abun da kai wani abun kake nema kuma? Tun na bar aikin a gidanka nake ta godiyar Allah daya sa na gane ku ne kuka zalince da wuri har na bar aikin a gidan, amman yau saboda rashin sa'a na sake haduwa da kai, tun da na zo gidan nan ba a taba duka na ba sai yau, a duk lokacin da na hadu da kai wani abun ne yake samu na marar kyau, bayan ka zalince a can nan kuma kana kokarin nuna min fin karfi, mi kake takama da shi? Duniya? Wani yana can ya fika arzikin be ma san da zaman ka a duniya ba, Wallahi duk arzikin da kake takama da shi wani yana can ko kan akaifarsa baka kamo ba, indan ka tara dukiya kamar karuna mutuwa za kai ka barta, ba za asaka ka kabarinki da naira biyar ba, na nice kai taimako zan yi da duniyar da zan amsawa Allah amsar inda da samo ta daga naira da kuma inda na kashe ta ba wai zalince ba,tir da mai dukiya irinka da zuri'arku tirr da dukiyar da zata rufewa mutun ido ya kasa ganin darajar dan 'adam din da Allah da kansa ya karrama....!” Tun da ta fara magana yake ta kallon cikin idanuwan, hawayenta na sauka da bugun zuciyarsa, ba a taba hasali kamar haka ba, wani beisa ya tsaya gabansa ya fada masa marar dadi kamar haka ya kyale shi ba, ransa be tana baci kamar haka ba, wata magana bata taba shiga cikin zuciyarsa ta saka shi raina kansa kamar yau ba, ba a taba kaskanta tashi kamar yau ba. Wani irin abu ya ji kamar ya dake ta kuma ba zai iya dukan nata ba, da ace yau wani tsaye agabansa ba Ataa ba ya fada masa bakar magana kamar haka babu abunda zai hana shi taka shi yadda yake so. Jin be ce komai ba sai kallonta da yake da jajayen idonwansa naman fuskarsa na rawa yasa ta juya da zimmar fice, sai ya kai hannunsaya fisgota ta juyo da ita ya nuna ta yatsa bakinsa na ta rawa kamar zai ce wani abu kuma ya kasa furta komai. Kamar wanda ya tuna wani abu sai yai saurin sakinta yana kallon hannunsa kamar mai kyama, ita hannun nasa ta kalla kamin ta kalli kafadar daya rika. “Gaskiya ne, be kamata ka rika ni ba, kar na saka maka talauci, talauciabun gudu ne na sani, ni kaina ba dan talauci ba da baka isa ka saka a cire kodar mahaifiyarta da matar da bakin likitan nan kuma na barku kuna yawo ba, ba dan talauci ba da baku isaku gan ni a wannan asibitin ba balle har ku zalince mu, da ba dan talauci ba da ba mu raba a kangon gidan babansu Rahma ba da har wulakanta mu, ba dan talaucin ba da baka isa ka shigo inda na ke kwana ka taka shi da kafafunka da suke da takalmi ba, ba dan talauci ba da ban zo aiki cikin gidan har a wulakanta ni ba, ba dan talauci ba da yau Mama Fulani bata daga hannu ta mareni ba balle yar ta kirani yar iska, komai saboda talauci ne komai komai ina nufin komai” Ta fada tana durkushewa a gurin ta fashe da wani irin kuka mai ratsa zuciyata. Kasa cewar komai yai yana ta sauraren yadda take rare kukan yana shiga har kasan zuciyarsa. Shigowar Mama Fulani da Muhseen ne yasa shi juyawa zai fito da idonta da suka gama renewa. “Mi kai mata Aliyu?” Muhseen ya tambaya cikin mugun bacin rai. Mama Fulani ta tari numfashinsa. “Mi yai mata? Wace irin magana ce wannan Muhseen? Ya wuce tai masa ba daidai ba ya mareta” Muhseen ya karasa kusa da Ataa ya dago hannunta yana kokarin ganin fuskarsa. “Who do you fucking think you're wai Aliyu? Kawai sai kai ta tunanin taka kowa yadda ka ga dama?” Juyowa Aliyu yai yana masa wani mugun kallo ya ce. “Saboda na isa ne ko akwai abunda za kai?” Muhseen zai yi magana Mama Fulani ta daga masa hannu. “Enough of this, saboda yarinyar nan yau fadan ku biyu, ya kuke abu kamar ba yan'uwa juna ba what?” Jin muryar Mama Fulani kamar zata fasa kuka yasa Aliyu saurin fita daga garejin cikin bacin rai kala biyu na Ataa da kuma na Muhseen. Motarsa ya nufa ya shiga ya dauki hanyar kamfaninsa, kana ganin yadda yake driving kasan yana cikin tsananin bacin rai. Duka ma'aikatan kamfanin sun yi mamakin ganinsa a wannan lokacin domin babu wanda ya san da zancen zuwansa balle kuma har ya shigo kamfani, he choose yaje kamfani sama da ya ji gida Rahma ta ganshi a haka ta zargi wani abu har ta kara bata masa rai. Duk inda yabi gaisheshi ake amman be amsa gaisuwar kowa ba har ya isa office dinsa ya saka katinsa kofar ta bude masa ya shiga ciki. A one of visitors chairs ya zauna yana jin kansa na mugun sara masa, kirjinsa kuma kamar zai fito saboda zafin da yake masa. Wani zafi yaji yana sauko masa da sauri ya tashi ya je ya kara gudun ac ya zo gaban teburin ya buga shi da karfi yana fitar da numfashi kamar wani zaki. Hannunsa yasa cikin gashin kansa ya matse kan sosai he tried to make himself calm, shi kansaba zai iya fadar ya fi saka shi wannan bacin rai a take ba, a cikin maganganun da Ataa ta fada masa ko wacce ta masa zafi amman ya fi jin zafin kukan da take fiye da maganganunta, and the way da Muhseen yake shige masa hanci yana bata masa rai, daman can shi da Muhseen basa shan inuwa daya. Freezer office din ya nufa ya bude ya dauko gorar ruwa mai sanyi sosai ya bude ya kafa kansa bakinsa ya sha rabi, ya zuba rabin a jikinsa saboda zafin da yake ji, haka yake ji a duk lokacin da ransa ya bace, sai dai ba karamin abu ke saka shi bacin rai kamar haka ba, sai an tona. Zuwa yai ya zauna a kujerarsa ya dauki files din gabansa yana dubawa, duka sababin files ne da be san da zamansu a office din ba kamin ya tafi. Telephone din dake gabansa ya danna. “Nasir same ni a office” “Office?” Nasir ya amsa daga dayan bangare, Aliyu be sake ce masa komai ba ya aje telephone din. Ko three minutes ba ayi ba na'urar da ke nuna isowar mutum ta fara kara tana fitar da danja ja, sai Aliyu ya kai hannunsa karkashin tebur din ya taba wani abu kofar ta rabe biyu Nasir ya shigo da saurinsa yana sanye da Suit. “Ban sa ran zaka shigo office daga dawowarka yau ba” “Ka kori mutanen nan, ba san aikinki su ba za mu iya daukar wata kaddara ba” Ya fada yana jefawa Nasir files din guda uku. Nasir ya duka ya dauka yana duba. “Dukansu sun kware akan aikin nan Aliyu wannan karon ne kawai aka samu matsala kuma kasan yanayin garin ai” “Fired them” “Idan muka koresu za mu dade ba mu maye gurbinsu ba” “I don't care fired them, kuma ka basu albashinsu” Nasir ya kalleshi da kyau sannan ya zauna yana fadin. “Fada min me ke damunka?” Aliyu ya mike tsaye yana ta huci ya nufi windows ya tsaya yana bude aninin rigar shaddar da ke jikinsa, sai kuma ya juyo ya kalli Nasir cikin bacin rai ya ce. “Yarinya karama zata fada min maganar banza? Yarinya karama?” “Ka samu ganinta?” “Na same ta a family home tana ma Mama Fulani aiki, ta fada min magana son ranta a yau, har abunda ban yi mafarki ba ta fada min and she called me azzalumi imaging” Ya karasa yana dora duka hannayensa a windows yana kallon wajen. “Duk shine ya saka wannan bacin ran? Aliyu dole fa kai hakuri iyakar zalinci fa an zalinci yarinyar nan, kuma abu ne mai wahala ta iya son ku a zuciyarta, idan har kana son ta daina maka kallon azzalumi dole ne ka fahimtar da ita, and show her your good side mana, wannan girman kan da fada da rashin tausayi duk sai ka aje shi a gafez zancen ta ji tsoronka be ko taso ba” Juyowa yai ya kalli Nasir “Ina da girman kai ne?” “Au baka da shi?” “Kawai dai na san bana daukar raini ne” “Amman miyasa ka damu da yarinyar nan ne har haka?” “Saboda kawai ta daina min kallon azzalumi ne, ko akwai wani abun bayan wannan?” “Kai ba ka sani ba ni ya za ayi na sani? Make yourself calm Aliyu, this is the right time da zaka taimake ta maybe ta yafe maka, idan mahaifiyarta tana nan kuje ku roki yafiyarta ku nema mata magani” Ya daga kansa sama yana ta mamakin kansa. “She got lucky wallahi, da ba ita ta fada min haka ba yau ko? Hmmm” Nasir yai murmushi. “Kuma ka damu ko? Ni Wallahi kai ke ba ni tausayi ba ita ba” Kallonsa kawai yai ya karaso gurin tebur din ya dauki keys dinsa ya fice daga office din. *Z A K I -it's not free, pay 300 to 0314795884 Abubakar Gt bank, then send the evidence via 08036126660* 21. Aliyu na fita Mama Fulani ta fice cikin bacin rai, sai ya rage dakin daga ni sai Ya Muhseen da ke ta rarrashina. “Fada min dukan ki yai?” “Be min komai ba” Na fada ina share hawayena idanuwana sun ji ja sosai, domin ba kadan nai kukan ba. “Be miki komai ba za ki yi kuka? Fada min gaskiya mana, dukanki yai ko?” “Be min komai ba, kawai kaina ne yake ciwo shine” “Za mu shirya da ke idan kin fada min abunda yai miki” Ya fadi hakan yana nuna ni sannan ya juya a fice cikin yanayin da ke nuna yayi fushi da ni. A ganina be kamata na fadi abunda zai iya zame min matsala, nasan idan har na fada masa dalilin kukan nawa wata kila zai iya tambayar mahaifiyarsa dalilin dukana da tai wanda hakan zai iya zama fada a tsakaninsu, idan kuma na fada masa abunda ke tsakanina da Aliyu abu ne da zai iya sakawa a koreni a gidan gaba daya ma, nai biyu babu. Tabarmar na daga na kabe saboda takawan da Aliyu yai sannan na sake shimfiďata na kwanta a kai ina saka hijabina na rufe kafafuna, sai ga Anty Maryam ta shigo garejin fuska a hade hannunta rike da wayar carja. “Ke uban wa kike wa rashin kunya? Ya Aliyu sa'anki ne?” Saurin tashi nai zaure a take jikina ya dauki rawa. “Ban masa rashin kunya ba” Ban gama rufe bakina ba ta watsar min wayar chajar a jiki iya karfinta, ban san lokacin da nai tsalle na dire ba, rabon da a saka wani abu a dake ni a jiki har na manta, amman yau saboda rashin gata na zo aiki gidan wasu yar gidan tana dukana akan abunda bata san gaskiyarsa ba. Haka ta bi ta bulale min jiki ko ina ta samu dukana take da wayar idan nai ihu ta ce na rufe mata baki. Ta fini girma da jiki sosai domin ita irin manyan yan matan nan ne masu kamar matan aure masu yaya shida, ba kamar Anty Rukaiya dake da karamin jiki ba. “Kuma idan na ji muryarki a waje sai na ci ubanki” Ta fada tana nuna ji da wayar da ke hannunta sannan ta fice ta barni a gurin ina ta murzar jiki ina hade kukana, duk inda ta bulalar ta same ni ya yi min ja kamar na jimu abun ka da mai farin fata, farin ma irin nawa mai ja sosai na jajayen buzaye. A gurin na kwanta ina ta hawaye, domin babu danar nai kuka sauti ya fita ta dawo ta kara min kamar yadda ta fada. Ana gaf da sallah magariba zazzabi ya rufe na rika jin sanyi na sauko min ga bulolin nata min zogi, kaina kuma yana ta ciwo har bana son daga idona. Ban iya fita karbar abinci a gurin Mama Fulani da Ammy ba, da yake kuma ba ni da gatan da wani zai da mu ban ci abinci ba babu wanda ya zo dubani ko a aiko min da abincin. Haka na kwana a gurin cikin rashin gata da galihu har gari ya waye, ina ta jin wuyar tashi amman ba ni da gatan da wani zai fanshe ni a aiki, na san ba ma za su yarda da uzurin cewar bana jindadi ba. A dan karamin madubin hoda ta na duba yadda idona da gefen kumatu na ya kumbura bulalar ta kwanta min har saman fatar ido. Wani ruwan hawayen ne ya sake cika min ido na fashe da kuka marar sauti ina ta jin kewar Nana da rayuwata da baya, na sani ba mu cikin jindadi amman a haka muke rayuwarmu babu wanda ya taba dukana, amman a nan ga duka ga wulakanci saboda kawai ina neman halalina. Ganin kamar zan bata lokaci ina kukan yasa dole na tsagaita kukan da ke kara min ciwon kai da damuwa na daura dankwalina na fito ina jin nauyin jikina saboda zazzabin da ke kara sauko min, na nufi part din Mama Fulani kamar yadda na saba, part din na fara gyarawa na ma komai tsaf sannan na nufi part din Ammy na gyara mata falonta, yanayi kawai ta lura da shi ta fahimci bana jindadi. “Jiya Fulani ta aiko ta ce karna baki abincin dare da safe, wani laifin kika mata hala?” Kaina kawai na daga na kalleta, ina bude baki nai magana sai kuka ya kubce min na saki tsintsiyar hannuna na durkushe a gurin ina ta kuka. Sai ta zauna a cushion tana ta kallona cike da tausayawa. “Mamana ki yi hakuri, duk wanda ya ce zai nemi halal dole sai yayi hakuri, musamman aiki a gidajen wasu, dole za ki iya haduwa da abubuwa da dama, ban san dalilin na aiki a nan ba, amman dai ki yi hakuri wata rana sai labari zai zama kamar ba ayi ba kinji” Na gyada mata kai ina share hawayena. “Baki da lafiya ne naga kamar fuskanki ya kumbura” “Kaina yana ciwo, kuma ina jin zazzabi” “Me mikai wa Fulani hala?” “Wallahi ban mata komai ba, kawai dai na fita ne bakin gate ina dawowa sai sai ta mare ni, kuma shine Anty Maryam ta dukeni da bulala” Na karasa ina kara fashewa da kuka. Sai ta girgiza kai cike da tausayawa. “Fulani bata da imani Wallahi, Allah ya kyauta” Tashi tai ta nufi upstairs bata dade ba ta dawo rike da kwayoyin magani ta bani. “Shiga kitchen ki debo ruwa ki sha” “Na gode Allah ya saka da alheri” Na fada ina saka hannu biyu na karba sannan na nufi kitchen kofi na dauka na debi ruwan na balle maganin sai na kasa sha, abun ka da wanda be saba ba, daman can magani da allura bana son su sai dole, daker na iya runtse ido na shanye maganin na fito ina ta bata baki, ko da na fito Anty Zee da Humaira, Inteesar da Batulu duk sun fito dakinsu, dan haka na shiga na gyara ko wane dakin da dakin Ammy sannan na fito. “Idan kin gama ki zo ki karbi abinci, amman karki bari ta sani” “To” Na amsa sannan na fito daga part din na koma part din Mama Fulani dan gyara bedrooms idan yayanta sun fito. Ko da na shiga duka yayanta suna dinning har Ya Muhseen, da alama da gaske fushi yake da ni domin ko inda nake be kalla ba, ba kamar yadda ya saba kallona ya sakar min murmushi ba, har na dauko tsintsiyar da mopper na shiga dakunansu na gyara komai na fito cikin rashin dadin rai na ke na fushin da na lura da Ya Muhseen na yi da ni, domin har ga Allah na damu kuma na ji babu dadi. Sai da gama gyara bedrooms din sannan na fito na sauko kasa, a lokacin Ya Muhseen baya dinning din ba kamar yadda na saba ganinsa idan na gama gyara an barshi a gurin zaune ba, wani lokacin ma shi yake miko min abincin na safe. Inda na dauki tsintsiyar na nufa na aje sannan na juyo da zimmar komawa part din Ammy na karbi abincina domin na san wannan Mama Fulanin ba bani za tai ba, sai na ji ta kirani. “Ke.... ” Na dawo da sauri na durkusa a gabanta cikin ladabi na ce. “Ga ni” “Shiga dakin Rukaiya da Maryam da Baby ki kwaso kayan durowarsu ki je garden ki wanke, ko daya karki bari kuma ki wanke su tas” Da to na amsa mata na taso ina tausayin kaina na nufi dakunnan na kwaso tulin wankin ko wanne zai kai kala goma sha biyar wani ma ashiri, sai da na kaisu garden din sannan na dawo na sake dukusawa a gabanta. “Ina sabulu” “Shiga store ki dauko” “Abincina fa?” “Sai kin gama wankin za ki ci ai tunda kika zabi rashin kunya sai na horaki a gidan nan” Ban sake ce mata komai ba na tashi na ahifa store din na dauko sabulun na nufi garden din, dana isa kurawa kayan ido nai na rasa da wanne zan fara wankewa? Shikenan saboda ba ni da gata duk abunda aka ga dama sai ayi min. Ba ni da wani iko da karfin da zan iya cewa ba zan wanke ba, dan haka na saka tufafin a gaba ina ta wankewa ga rashin karfin jiki na zazzabin da na ke ji, ga yunwar jiya da dare gashi da safen nan ma ban saka komai a cikina ba. Haka na saka kayan a gaba ina ta wanki tun ina yi da dan kuzarina har na koma bana iya komai na gaji sosai amman a haka na tisa kayana a gaba na wanke su tas babu abunda na bari, sannan na bi na shanya su, sai na zuba ruwa robar na laba bayan itacen mangoro guda biyu da suka hade waje daya na boya a gurin nai wanka wai ko zan dan samu karfin jiki, sai dai abunda ban sani ba Ya Muhseen na daga dakin Mama Fulani yana hange ni, sai dai a lokacin da nake wanki ban ganshi ba, wata kila be zo gurin ba sai da na fara wankan, kuma ban lura da shi ba sai da na gama wanka. Kunya ce ta kamani duk sai na ji babu dadi ko ba komai yaga tsiraicina wanda shi kansa na san yasan haramun ne, ban tsaya saka rigata a gurin ba, na dauketa tare da dankwalina na fito daga garden din na nufi garejen, a cikin tufafin Inteesar da Ammy ta bani na dauki wani lace na saka na daura dankwalin sannan na nufo part din Mama Fulani dan bata ragowar rabulunta. ALIYU POV. A lokacin daya bar kamfani sai ya dauki hanyar gida, yana ta tunanin maganganun Nasir, tabbas shi kanshi ya san an cuci yarinyar kuma dole zara ji zafi saboda mahaifiyarta akai wa, but he like yadda take fada masa magana kai tsaye ba tare da tsoro ba, idan ya tuna ko wace kalma ta ta sai ya tsinci kansa a kogin tausayinta, yes she's right da ace yar masu hannu da shuni ce da Doc Asim be yarda ko yatsanta ya taba ba balle har ya cire kodar mahaifiyarta, and secondly na ji zafin hawayen da ta zubar da cewar da tai Mama Fulani ta mareta, yasan Halin Mama Fulani daman ba jutuwa take da yan aiki ba, shiyasa duk wacce aka kawo da taje ganin gida bata dawowa, a dayan bangaren kuma yana jin haushin yadda Muhseen yake masa. Iya kokarin da yai ta isa gida ba tare da Rahma ta gane yana cikin damuwa ba, ko da ya isa ya sameta a falo dinning mai dafa musu abinci namiji yana serving dinta, yana daya daga cikin dalilin daya saka take son zama a Abuja a nn ko kofi bata kawarwa mai musu aiki ne namijin dan kabilar igbo yake mata komai ciki kuwa har da dafa abincin da gyara duka dakunan. Juyowa tai ta kalleshi da far'a da alama tana cikin farinciki. “Dear welcome” Karasawa yai kusa da ita ya kai bakinsa ya sumbanci gefen kumatunta sannan yaja kujera a kusa da ita ya zauna. “Na yi waya da Doc Perry gobe zan je na ganshi” Shiru nai na wani dan lokaci sannan ha kalleta. “Why ba zaki bari sai nan da kwana biyu ba idan kin huta” “Ba wani zancen hutu, tunda yanzu na samu lafiya ai zan iya komai, kara kawai na maida hankali gurin neman haihuwar” Ya gyada mata yana mikewa tsaye kamar be jidadin. A daren da tunani biyu ya kwana a ransa, na ganin Doc Perry da Rahma ta ce za tai da kuma na Ataa wanda be san dalilin na damuwar kansa da tunaninta ba. Ko da suka tashi da safe mai dafa musu abinci ya gabatar da komai a beburin karyawa, a tare ya karya da matarsa sannan na ya shiga dakinsa ya shirya cikin shiga ta manyan kaya ya fito yai mata sallama ya kama hanyar kamfaninsa. A kamfanin ya wuni duk wani abun da akai baya nan sai da aka gabatar masa da shi ya ganshi kuma ya duba yadda komai yake tafiya kowa ya san da cewar oga ya dawo sannan suka shiga meeting, bayan sun fito ne yake labartawa Nasir zancen ganin Doc Perry da Rahma zata je yi. “Then why da ba zaka fada mata gaskiya ba? For how long za kai ta aje wannan sirrin ne Aliyu?” “Ban sani ba, iyakar abunda na sani zan iya ajiyarsa har karshen rayuwata, kawai kasa a nemo min Doc Perry ina son magana da shi” “Haka zaka daukarwa kanka a duk lokacin da zata je ganin wani likita sai ka samu kudi ka bashi a rufe maganar? Anya hakan zai haifar maka da da mai ido Aliyu? Idan ma kai baka son ganin iyalinka ai familynka suna so, muma kuma muna so” “Matata tana da muhimmanci a gareni Nasir, idan ta san gaskiya ni ne zan fi shiga damuwa domin zata saka kanta a damuwa ne, kuma duk abunda nai mata zata ga na mata ba daidai ba, and kasan Mama Fulani ma zata fara damunta just like Momy daman can ba jutuwa suke da Momy ba” “Amman wannan kawai ya isa ka kasa kanka a wannan matsalar? Kana ganin idan kai ne Rahma zata zauna da kai? No ina da Tabbacin duk yadda take son ka ba zata zauna da kai ba, shekarar ku takwas da aure Aliyu idan baka fara tunanin samun haihuwa a yanzu ba, zuwa yaushe zaka fara? Lokaci yana tafiya, a yanzu nan gaba kadan karfin ragowa zai yi ba karuwa ba, ya kamata kai tunani” Aliyu ya tsaya cikawa bakinsa iska a lokacin daya riga Nasir shiga office din. “Kamin na ga wasu yayan Rahma na fara gani, be kamata ace wani abun ya shiga tsakaninmu ba” “Haihuwa ita ce shiga tsakani? Kai ba haihuwar ka akai ba?” “Yes i mean kasan yanzu idan kowa ya gane gaskiyar Rahma zata shiga matsala ta shiga damuwa, kuma muna son junanmu ni da ita, be kamata abunda be riga ya zo ba ya saka mu damuwa” “Ina da tabbacin da akanka ne Wallahu Rahma ba zata zauna da kai ba, zata fi son ganin gudan jininta fiye da kai, ballantana tana ganin cewar tana yar nai nera zata iya samun wani mai nera ta aura” “Baka san yadda Rahma take so ba ne Nasir baka san so ba ne” “Fine, idan kana son ka gane gaskiya ka daina cewa kai da ita ba ku da matsala, ka fada mata cewar kai ne mai matsalar wannan karon idan kunje tare ka biya Doc Perry ko nawa yake so ya fada mata haka, na tabbatar zaka ba ni wani labarin dabam” Aliyu yai shiru yana nazarin kalaman Nasir. Ta wani bangaren yana ganin kamar be dace ya gwada Rahma kamar haka ba, wani bangaren na zuciyarsa kuma yana ta zugashi akan ya gwada din. Har ya bar office din be samu matsaya daya akan gwadarwa ko kin gwadarwa ba, ya sa dole zata kira shi tace mishi tana asibiti ya sameta a can a gwada lafiyarsu ta bangaren haihuwa kamar yadda ake musu a ko da yaushe, sai dai ba shi tabbaci ko Doc Perry zai yarda da hakan ba har ya aikata domin shi babban likita da kowa ya san da zamansa cikin garin Abuja, matukar kana amsa sunan mai nera to ka san Doc Perry, likita daya kware akan aikinsa kuma yake fadin gaakiya a ko da yaushe, ba iya nan kawai yake duba mutane ba har kasar waje an san da zamansa, sai dai Rahma bata taba damuwa da su je gurinsa ba, sai a yanzu da haihuwar ta fara damunta. A hanya yai sallah la'asar sannan ya isa family house gurin wato gidan Alhaji Hamza. A harabar gidan yai parking amman be fito cikin motarba ya tsaya dannen dannensa har ya hango Ataa ta fito daga Garden daga ita sai daura gaba, kirjinta a cike ga farin daya bayyana kansa a jikinta, gashin kanta a jike da alama wanka tai ko kuma ruwa ta fada, amman idan ruwa ta fada ai dole har tufafin jikinta zai jike, be taba kula da surar mace karamar yarinya kamar yadda ya kula da ta Ataa yau ba, karamar yarinya ce amman tana da abunda yake kauna a jikin mace wato breast ga yawan gashin kai, wanda ko Rahma da take babbar mace bata kaita breast ba, ga gashin kai kamar wacce akai wa dashe ya kwanta har gaban goshinta gwanin sha'awa, and every takunta jikinta motsawa yake fatarta na sheki kamar mai shafa wani kasaitaccen mai. Kasa dauke idonsa yai daga kanta har ta shige garejen ba tare da ta kula da shi ba. “Miyasa tai wanka a Garden?” Ya tambaya kansa cike da mamaki kamin ya tuna da cewar ai babu bandaki a garejin. Then miyasa ba a aje ta BQ ba? Ya sake tambayar kansa sai dai wannan karon a zuci yai tambayar kamin ya hade yawun bakinsa ya bude motar ya fito ya nufi part din Ammy sai da ya fara gaisawa da ita kamin ya shiga part din Mama Fulani. A falo ya samu kowa ban da Muhseen, Maryam da Rukaiya na ganinshi suka natsu sosai ko motsi kirki basa yi, cikin mutumci suka gaishe shi ya amsa musu kamar yadda ya ba fuska a daure sannan ya gaishe da Mama Fulani ita kan fuska a sake. Be yi zaman mintuna biyar ba Ataa ta shigo falon sanye da wani milk lace wanda ya kara fito da kyau sosai sam ba zaka ganta a hanya ka za ci yar talaka ce ba, lace din ya kara fito da kyauta da jan fatarta sosai ta yi mugun kyau duk da kasancewar bata shafa mai ba balle ma hoda haka ta fito naturally beautiful. Kasa dauke ido daga kanta Aliyu yai yana ta kallonta kamar yau ya fara ganin mace mai kyau, yanayin tausayin da ke fuskarsa yasa shi jin tausayinta ba tare da wani dalili ba, q nan ya lura da tabon bulalar da ke fuskarta da kuma kumburar da fuskar tai da idonta, tafiya take kamar zata fadi saboda rashin karfi na yunwar da take ji. Tana karasowa gaban Mama Fulani ta zube tana mika mata ragowar sabulun da ke hannunta. “Gashi na gama wankin na wanke dika” Ta fada cikin wata sautin murya daya saka tsigar Aliyu tashi. “Je kitchen ki aje” A nan Ataa ya hade hannayenta ta kama kafafun Mama Fulani ta rike ta fashe da kuka. “Ki taimaka min dan girman Allah ki ba ni abinci yunwa na ke ji kamar na mutu....” “Bata ci abinci ba?” Aliyu ya tambaya yana kallon yadda hawaye suke sauko a idonta kamar ba gobe. “Ai tun jiya da tai maka rashin kunyar nan ban bata abinci ba, kuma na fadawa Ammy karka bata, na sa Maryam ta zane mata jiki, kuma yau na hada ta wankinsu tun safe sai yanzu ta gama, haka zan rika mata tun da ta zabi yi ma mutane rashin kunya” Wani irin abu yaji na rashin jindadi yana ratsa zuciyarsa a take tausayinta ya rufe shi, how old she's da za a ace tai wanki tun safe har la'asar and an a hana mata abinci kuma a saka Maryam ta dake ta duka saboda shi, a tunanin Mama Fulani rashin kunya tai masa shiyasa ta yanke mata wannan hukuncin. “Ke zubo mata abinci” Ya fada yana kallon Rukaiya, da sauri ta tashi ta nufi kitchen din ta zubo mata abincin a plate ta kawo sai ta tsaya gabanta. “Tara dankwalinki a zuba miki ko kuma ki je ki dauko plate dinki” “Bata da darajar da zata ci abinci a plate din ne? Give it to her....!” Ya dakawa Rukaiya tsawa, da sauri ta mikawa Ataa plate din, cikin wani irin rawar jiki Ataa ta karbi plate din ta aje a gabanta ta saka hannu biyu tana cin abincin da su bata iya hakurin har ta cinye da dama ta sake debowa saboda azabar yunwar da take ji, sai dai idan ta ci da dama ta ci da hagu bata ma tsayawa tauna abincin sai dai kawai ta hade, jikinta na ta rawa sosai. Wani irin tausayinta ne ya rufe shi, ko ba komai saboda abunda akaiwa mahaifiyarta take aiki a gidan saboda ta sama mata magani kamar yadda ta fada masa, kuma sune silar ciwon mahaifiyar kusan shine silar komai ma, domin ko dukan da Mama Fulani ta saka Maryam tai mata ai saboda shi ne, iya kar abunda yake jin zai iya yi a yanzu na taimakonta ne ta samu saukin rayuwa a gidan kamin ya karkato da hankalinta har ta yarda ya taimaki mahaifiyarta ya nema mata magani. “Mama pls karki sake horata da yunwa” Ya fada cikin taushin murya kamin ya kalli Maryam yana mai jin haushi na rashin dalili cikin kakkausar muryar ya ce. “Karki sake dukanta, tun da ba yar ki ba ce” “To Ya Aliyu” Ta amsa da sauri sannan ita da Mama Fulani sukai kallon kallo, mamaki ya gama cika su gaba dayansu. Wani bakin haushi da bacin ran abunda akai ma Ataa ya rufe shi, ga kuma tausayinta a bangare daya, yana ta kallon yadda take auna abincin a bakinta kamar wacce bata taba cinsa ba sai yau. Tsarkiwa tai ta fara tari tana ta wani abu kamar za tai amai saboda cikinta daya kulle. “Kawo mata ruwa” Ya fada yana kallon Maryam da mamaki ya kusa kashe a inda take zaune. Tashi tai taje ta debo mata ruwan na fonfo ta kawo mata Ataa ta saka hannu biyu ta karba. “Na gode” Ataa ta fada sai ta kafa bakinta ta shaye ruwan gaba daya. Tana dire kofin Sulaiman Mai ban ruwan fulawoyin gidan ya shigo da sallamarsa, aka rasa mai amsa sai Aliyu saboda kasaita kowa ganin yake ba zai iya amsa sallamar wanda yake kasa da su ba. “Wai Kamal ya ce yana sallama da Aisha” Aliyu ya kalleshi Mama Fulani da sai yanzu ta samu damar magana ta ce “Aisha ko Maryam dai?” “Aisha dai ya ce” “Ba mu da Aisha a nan gidan” “To” Ya tashi da sauri ya fice, sai kuma ga shi ya dawo ya sake zubewa kasa kamar dazun. “Ya ce wai Aisha mai aikin a nan gidan Ataa” Mama Fulani ta kalli Ataa da bata san wainar da ake toyawa ba sai aikin aika abincin take a bakinta sannan ta kalli Sulaiman ta ce. “Wane Kamal din wai?” “Kamal dai soja wannan makocin mu” “Ya ce yana kiran wannan yarinyar” Mama Fulani ta fada tana nuna Ataa da tsananin mamaki. “Haka dai ya ce” “Tashi ka yi tafiyarka” Aliyu ya fada masa sannan ya mike tsaye ya bi bayansa yana wani irin taku na kasaita da isa. Mama Fulani ta kalli Maryam. “Wai ko dai manta sunanki yai?” “Hmmm Wallahi ba wani mantawa kyau ne yake rudarsu, ba ki ganin wannan yarinyar kamar aljana” Rukaiya ta fada tana kallonta, sai Mama Fulani ta kirata dan kara tantancewa. “Ke” Ataa ta dago ta kalleta. “Na'am” Mama Fulani ta kura mata ido tana ta kallonta kamin ta gyada kai. “Eh lallai ko ba shakka” Maryam taja tsaki. “Shegiya mai kama da mayu, duk sai na yanke gashin kan nan” Ataa dai bata ce musu komai ba, da ta gaji da yadda suke ta hantararta sai ta tashi ta fice daga falo dauke da plate din da cofin ruwan domin ta san Mama Fulani ba zata taba son kayan ba tun da ta yi amfani da su. *Z A K I -it's not free, pay 300 to 0314795884 Abubakar Gt bank, then send the evidence via 08036126660* ZAKI By Khadeeja Candy 22... Ya Muhseen ya gyara tsayuwarsa yana kallon da mugun mamaki. “Me kake nufi? Dan iska ne ni?” “Ko ma dan ruwa ne kai ta shafa” Aliyu ya fada mishi sannan yai min alama da na zo na wuce da ido, komawa nai cikin na dauko mopper da tsintsinyar na fito, duk irin rashin tsoron sa da nake yanzu kan na ji tsoron yadda na ganshi na san zai iya min wani abun ko kuma wani fadan ya shiga tsakaninsa da Ya Muhseen wanda a karshe ni ce aciki domin ni za a daka. Sai da na fice sannan ya biyo ni a baya ina ta sauri kar ya cin min har na shige part din Mama Fulani, sai gashi ya shigo cikin tsannanin bacin rai. “Mama” Ya kwala mata kira sai gata ta fito daga kitchen din da sauri. “Mama kar yarinyar nan ta sake shiga part din Muhseen da sunan gyara masa daki, idan a cikin kanennsa ba zai saka wata tai masa ba ya hakura da gyaran kawai” “Cewa kikai ya miki wani annmimiya?” Mama Fulani ta fada, nikan tuna har na fara kuka domin na san ni za a dorawa laifi. “Bata ce ba, ni dai na ke ganin rashin dacewar hakan tun da ba muharramarsa ba ce” Da mamaki Mama Fulani ta kalleni ta kalli Aliyu sai kuma ta kalli Muhseen da ya shigo yanzu cikin bacin rai. “Kai wani abun ka mata?” “Ban mata komai ba, yadda yake dan iska haka yake tunanin kowa ya ke” “Ni ba dan iska ba ne ka fi kowa sani” “Then why ni zan zama dan iska? Ba uwa daya ta raine mu ba? Kai baka iya kyautatawa kowa zato? A yadda kaga dama haka kake son taka mutane? Ba zai yiyu ba Wallahi idan zaka taka kowa yadda kake so a gidan nan ni kan ba zaka iya da ni ba, sai dai bakincikina na kashe ka” Aliyu be sake cewa Muhseen komai ya zauna a sofar da ke kusa da kofar yana ta huci kamar wani zaki. “Zan baka mamaki Aliyu kuma fadan yanzu muka fara ni da kai” Mama Fulani ta karasa fito daga kitchen din tana girgiza kai. “Haba Muhseen? Haba Aliyu wannan wace irin rayuwa ce” Aliyu ya dago ya kalleta. “Mama miye laifina dan na ce kar a barshi ya kebe da wacce ba muharramarsa ba? Yarinya mai jini a jika kamar wannan za ki turara dakinsa ace ta share?” “Kai muharramarka ce da ka kebe da ita jiya a Gareji? Waya san abunda kai mata take kuka?” “Muhseen....!” Mama Fulani ta daka matsa tsawa. “Mama ba za mu taba shiryawa da wannan mutumen ba matukar ne dauke wannan girman kan da son milkin kowa ba, ba zai yiyi yace zai juya kowa yadda yake so ba, ba a karkashinsa na ke ba, dan haka ba zai yiyu ya ce zai juyani yadda ya ke so ba” Mikewa Aliyu ya ya fice daga falon cikin wano irin zafin rai marar misaltuwa. Mama Fulani ta nufo inda na ke tsaye zata dake ni. “Zo nan bakar munafuka ai duk ke kika hada komai” Sai Ya Muhseen yai saurin tsakaninmu ya tare ni. “Karki da ke ta Mama, za ki dauki alhakinta ne kawai, ba ki iya ganin laifin Aliyu sai dai wasu, bayan kuma shi ne mai laifin, kuma Wallahi sai na bashi mamaki” Ya fada sannan ya juyo ya kalleni. “Wuce daga nan” Da saurina na fice daga falon har ina tuntube kamar zan fadi, abun ka da mai shegen tsoro haka nai ta kwara ido a garejin ina ta jiran wani daga cikin yayanta ko kuma ita kanta ta zo ta dake ni amman shiru babu wanda ya zo har dare yai, ban fita karbar abinci a part din Mama Fulani ba, sai na je part din Ammy a can na ci abincin dare na sannan na dawo garejin na kwanta abuna na kwana har safe. Kamar yadda na saba da wuri na farka ina gama sallah na shiga na gyara falon Mama Fulani sannan na je part din Ammy na gyara kamar yadda na saba, bayan na gama Mama Fulani ta ce na dauko gurina aka zuba min abincina, har zan fito sai ya Muhseen ya kirani ya kara min da na shi na fito ina ta murna, a garden na zauna na cinye abuna sannan na dauki plate din naje na wanke na kawo gareji na aje. After like one hour Rukaiyah ta shigo garejin tana rike da makullin mota. “Ke ta so muje ki riko min kaya” Da sauri na taso na biyo bayanta a zato daga mota zan riko mata su ko kuma a cikin gida zan dauko na saka mata a mota sai na ji ta ce. “Ki shiga gidan baya” Juyawa nai da zimmar komawa gareji na dauko Hijab dina sai ta daka min tsawa. “Ke ina za ki je?” “Hijab dina zan dauko” “Ba Hijab ba ubanki shiga mota muje” Da sauri na nufi motar na bude na shiga daga ni sai lace dina na jiya da sai dankwali, sai da na rufe motar sannan ta shiga mazaunin direba ta tashi motar muka fice, ni dai ina zaune a baya ina ta kalle-kalle har muka isa wani katafaren shago irin wanda na ke gani a tv nan, wanda komai da komai ana saida a ciki kuma komai bangaren dabam, ni kallo ya hanani rufe motar har sai da naji an dangware ni da karfi. “Bakauyar banza rufe min mota” Sai na saka hannu biyu na rufe. Na bi bayanta muna ta taka dan karamin matakalin har muka isa gaban babbar kofar wacce wasu masu uniform suke budewa mutum idan zai shiga, wani dan kwando taja ta mika min shi. “Ja wannan mu tafi duk abunda na nuna miki ki dauka” Na saka hannu na karba ina turawa, wai ita ala dole sai ta nuna ni din yar aikin gidansu ce ta sha wani bakin gilashi a fuska tana sanye da yadi babu mayafi a jikinta, ni kuwa duk sai naji na takura da rashin mayafin duk kuwa da na lura kusan rabin matan da suke shigowa shopping din basa da mayafi kuma kowa be kula ba, duk inda muka bi kallona ake nasan wannan baya rasa nasaba da gashin kaina da nai masa tsoro daya na ya sauko har gurin mazaunaina, da kuma haskena ga kyau kamar wata balaraba. Turin kwandon be dame ni ba dan ji nake kamar ina tuka mota duk inda na ga dama juyashi na ke ina jindadi. Dauko wannan dauko wancan haka take bani umarni ina bi kamar bawa da uban gidansa, muna isa sashen kayan dadi ta umarce ni na dauko madara ina kai hannuna sai na ji an rike hannun, da sauri na kalli gafena. “Na kama ki” Kamal ne sanye da kananan kaya fuskarsa da murmushi kamar kullum ni ma Murmushin nai sai kuma nai saurin kallon Rukaiya wacce ita ma murmushin take sakar masa. “Rukaiya shopping kuka zo” “Eh Wallahi har ma mun kare daman ba da yawa zan yi ba ya aikin?” “Lafiya kalau, sai ki ba ni aron Mamanar tawa ta raka ni shopping tun da kun kare, kadan na gama sai mu koma gida tare” Sakin baki tai kamar zata ce masa ba mu kare ba, sai kuma ta ga kamar be dace tai karya ba, dan haka tai murmushin yake. “Ba matsala” 24 “Thank you, idan kin je gida ki fadawa Mama Fulani ni na areta kuma zan kawo ta nan ba da jimawa ba” “Okay ayi shopping lafiya” Taja kwandon daga hannuna tai gaba a abunta kamar tana jin haushi. Sai da ta wuce sannan ya dawo da dubansa gurina ya ce. “Shiga ciki na turaki” Ba shiri na bude baki. “Aa mutane suna kallon mu, kuma mutane ba sa shiga cikin kwadon zuba kaya ai, za su mana fada” “Ko?” Ya fada yana murmushin kan na sake cewa wani abu ya dauke ni ya zuba a cikin kwandon yana dariya, ina kokarin fitowa ya girgiza min kai. “Karki fito basa fada” “Ni kunya na ke ji” “Nan Abuja ce ba ruwa kowa da kowa” Tura ni ya fara yi yana tafiya yana dauko duk abunda yake so yana sakawa a gwandon. “Fada min abunda kike son na siya miki” “Bana son komai” “Kina son abun goge baki? Ko kadar mata ko turare?” Na yi shiru ban ce komai ba sai yai murmushi ya fiddo wayarsa ya dauki ni hoto. “Bari na taimaka miki na saka ki a status dina ko wani zai gani ya zo kawata” “Kawarka? Mace?” “Eh mana” Saurin sauka nai daga cikin kwandon duk na san wasu sun gama gani na domin ya zaga wani bangare na shopping din da ni a ciki har wasu na kallona. Da kanshi ya koma yana tura kwadon duk wani abun kwadayi daya gani sai ya dauko guda biyu ya fasa ya ci ya bani rabi sai kuma ya saka rabi a cikin shopping basket din. A haka ya daukar min kadar mata da turare da man goge baki sannan muka zo gurin biya ya ciro kudi mai yawa ya bada sai suka saka masa kayan a leda wani daga cikin yaransu suka zo suka dauka suka kai masa a mota. A tare muka fito daga shopping din yana cin chocolate. “Na jidadin zuwa shopping din nan kin ga na hadu da ke, jiya na aika kiranki waya hana ki fito?” Nan ma shiru nai masa ban ce masa komai ba, sai ya bude min gidan gaba yana fadin. “Shiga muje yau dai sai kin ba ni labarin abunda ya kawo ki garin Abuja” Sai da na fara taka wani abu dake gefen murfin motar sannan na shiga cikin katuwar motar mai tuli sosai, sai shi ma ya zagoyo ta mazaunin direba ya zauna ya rufe motar yana kunna ac motar tare da kai hannu ya rage karar sautin da ke tashi sannan yaja motar muka hau babban titi yana ta kallona kamar ba driving yake ba. ZAKI By Khadeeja Candy 23... Kamal na tsaye yana lasar wayarsa yana jiran fitowar Ataa sai ga Aliyu ya fito yana wani shan kanshi, bayansa Kamal ya rika kallon a zatonsa ko tana bayansa ne amman sai yaja gate din rufe bata fito ba. “Kai kake kiran Ataa ne?” “Eh nine Aliyu ya aiki, ashe ka dawo” Kamal ya fada yana mika masa hannu. “Yes, wani abun ta maka ne?” Da mamaki Kamal ya sake kallon Aliyu sai kuma yai murmushi. “Mi zata min bata min komai ba” “Miyasa kake kiranta?” “Mun saba gaisawa da ita ne kwana biyu, yau kuma ban ganta ba, shiyasa na aika a kira min ita, da wata matsalar ne?” Aliyu ya tsaya kallonsa kamar ba zai yi magana ba can kuma ya ce. “Babu, idan gaisuwa ne, ba sai ka kara aikawa nemanta ba aiki take, aikin da aka kawota dan shi” Aliyu na fada masa haka be tsaya jiran abunda zai kara cewa ba ya juyo ya dawo cikin gidan, cikin wani irin jin haushi da be san dalilinsa, a dayan bangaren kuma yana jin idan har ya kyale rayuwar Ataa zata iya shiga wani hali domin kyanta zai rudi samarin su fara jan ra'ayinta ga wata hanyar da dabam wacce bata dace ba. Cikin falon ya dawo ya zauna sa dai be samu Ataa a falon ba sai Mama Fulani da Maryam da Rukaiya suna wata magana ganinsa sukai shiru. “Lafiya yake nemanta?” “Lafiya kalau, wai zuwa yai su gaisa” “Su gaisa?” Mama Fulani ta tambaya da mugun mamaki. “Shi Kamal din? Kuma ya tsaya a waje?” “Ai ba zai shigo ba dan kar mu dauka gurin Maryam ya zo tunda gurinta ya saba zuwa shiyasa ya aiko a kira masa wannan kazamar” Rukaiya ta fada tana yatsina fuska, Mama Fulani ta ce. “Ni fa tun ranar na ke ta mamakin ganinsa har cikin falon nan, domin abu ne mai wahala ya shigo cikin gidan nan idan ba Aliyu ya zo nema ba, sai kuma Maryam wani lokacin idan yana son su gaisa” Aliyu ya kalleta kamar ya ce wani abu sai kuma yai shiru ya maida hankalinsa gurin tv. Rukaiya da Maryam kuma suna ta kallon juna alamar gulma na cikin cikinsu tana cin su. Wayarsa yai jit alamar kira sai ya cirota daga aljihunsa ya duba number Rahma ce, hakan yasa shi picking ba tare da bata lokaci ba. “Dear karfe tara za mu je mu ga Doc Perry, idan baka gida ka same ni a asibitinsa idan kuma ka dawo da wuri sai ka same ni a can” “Kun yi magana da shi ne?” “Eh mun yi karka bata lokaci ka ji?” “Na ji make sure kin ci abincin dare kamin ki tafi” “Okay i love you” Be amsa ta ba ganin cewar yana a gaban Mama Fulani sai kawai ya kashe wayar ya tura mata ta sako. Ko be fada ba Mama Fulani ta san da Rahma yai waya, sai dai abunda bata gane ba ta ci abincin kafin ta tafi. “Ina zata ta fi?” “Zamu je mu ga Doc Perry ne” “Ciwon ya tashi ne?” “Aa akan matsalar haihuwa ne” “Hmmm haka za ku yi ta bata lokaci da kudin a banza ba ku samu mafita ba, na sha fada maka idan ba aure ka kara ba ba zaka taba haihuwa ba” “Ni da ita duka likitoci suna cewa ba mu da wata matsala za mu iya haihuwa a ko yaushe, wata kila lokacin ne bai yi ba” “Idan lokaci be yi a yanzu b yaushe zai yi? Shekara takwas fa, haba abun nan yayi yawa” “To ya za'ayi haka Allah ya kaddara” “Aa Wallahi ba za mu gane haka Allah ya kaddara ba, sai ka kara aure mun ga ita ma wacce ka aura bata haihu ba tukuna sai mu san yin Allah ne, amman dan ance za ku iya haihuwa a ko da yaushe ai ba abun dogara ba ne” Yai dan murmushi “Mama Rahma fa bata son kishiya” “Ni son kishiyar na ke da aka min ita? Ko kaunar Ammy na ke aka ce maka? Amman a haka na hakura na zauna da ita gata nan ta zuba zuri'a arzikina ma bata haifi namiji ko daya ba, sai ita wannan dan ta auri sarkin soyayya zai ce ba zai kara aure ba dan bata so ko? To baka isa ba, ni ba zan dauka ba idan kai baka son ganin zuri'ar ka ni ina so” Juyowa yai ya kalleta da kyau. “Idan kuma na kara aure ya zama matsalar daga ni ne fa?” “Sai mu a cigaba da neman magani, amman ai yanzu ba za a gane ba sai ka kara auren, ba fa zan yarda ayi ta tafiya a haka ba har mu zo mu mutu ba mu ga yayanka ba” Tana kaiwa nan ta mike tsaye ta nufi upstairs. Da kallo Aliyu ya bita har ta haye sannan ya kawar da kansa ya sauke ajiyar zuciya daman ya san Mama Fulani bata masa da sauki idan aka tabo bangaren haihuwa shiyasa ko da yaushe yake kokarin ganin ya kare Rahma, amman a yanzu dole yai ma tufkar hancin ko dan saboda Mama Fulani a yanzu yake ganin ya dace yai amfani da shawarar Nasir na maida matsalar a kansa shi kadai, sai da ya shafa kansa sannan ya mike tsaye ya fice daga falon zuwa part din Ammy domin ya gaisa da ita. ATAA POV. Dana soma tsarguwa da yadda suke kallon suna aybanta ni ne yasa na tashi na tashi na bar musu falon na dawo garejin na zauna na karasa cin abincin, sai da na cinye shi tass na koma ina tsude kwanon da kuma hannuna abincin ko dadi babu dan kawai ina jin yunwa ne domin abincin Ammy ya fi na Mama Fulani dadi, da na gama sai a dauki plate din da cup din na nufi garden na wanke tare da tara wasu ruwan na sha sannan na dawo garejin na kife su guri daya da wacan plate din da Mama Fulani ta bani da farko, ni ina ruwana da kymarta ai na kara samun wani plate din da cup, sai da na jerasu sannan na kwanta a gurin ina jin gajiya na sauko min. Kamshin turaren Aliyu da na ji ne yasa na dago kaina na kalli kofar shigowa garejin sai na ganshi a tsaye yana kallona fuska a hade kamar na masa wani abun, har harara na watsa masa na turo baki kamar yadda na saba idan ina fushi na juya masa baya na kama tsorona ina ta watsa da shi. “Idan Kamal ya sake zuwa nemanki a gidan nan sai na bata miki rai” “To ni na ce ya zo nemana? Ni ina ruwana” Yana fada a take na bashi amsa ba tare da na juyo ba, har sai da na ji kamshin turaren na shi na kara matsoni alamar ya baro gurin kofar ya nufo inda na ke kenan, sai nai saurin tashi zaune still bakina a ture ina kallonsa har ya karaso. “Kar na sake ganin kin yi wanka a garden” Ya fada yana zare min ido, ni ko kuwa be san bana jin tsoronsa ko kadan a raina ba. “To ina kake son naje nai? Idan na yi wanka a wani gurin sai ga a ce na yi ba daidai ba dake ni ko? Ni ba zan iya wanka a bandakin wani kato ba ace kullum zan yi wani abu sai dai na je bandakin mai gadi nai ni ba zan sake yin komai a can ba” “Tashi ki koma bq a can za ki rika kwana” “Ba zan koma ba, ni babu inda zan je, matar gidan a nan ta aje ni dan haka a nan zan zauna ba zanje ko ina ba” Na bashi amsa kai tsaye ba tare da fahimtar inda yake nufin naje ba. Matsowa yai kusa da ni ya kai hannunsa ya rika gashin kaina ya matse shi sosai ya mikar da ni tsaye da shi yana kallon idon cikin wani irin bacin rai ya ce “Idan ina magana kina ba ni ko wace amsa sai na ballaki” “Ka balla ni mana, ka balla mahaifiyata ai, ka gama da ni daman, kadan ya rage kuma sai ka karasa ni a yadda kake so ai, ba zan taba tsoron ka ba Aliyu, ba zan taba kaunar ka ba, ba kuma zan taba kyale ka ka fada min magana daya marar dadi ba, ko wace magana da zaka fada min ina da amsarta, ba zaka cutar da mahaifiyarta kuma ka sake cutar da ni ba, azzalumi kawai kai da yan'uwanka ba ku iya komai ba sai zalinci sai danne hakkin wanda kuka fi karfinshi sai cin amana, Wallahi Allah sai ya saka min a ko wane zalinci da kuka min, kuma matarka ba a zata taba lafiya ba har abada” Ina fada yana matse min gashi da dukan karfinsa har sai da na fashe da kuka sannan ya sake ni na fadi a gurin na fashe da kuka. “Mugu” Daf da zai fice na fada masa haka sai ya juyo ya kalleni da cat eyes dinsa, sai kuma ya juya ya fice ba tare da ya sake cewa komai ba. Be yi minti biyar da fita ba sai ga Inteesar ta shigo garejin. “Ataa wai Ya Aliyu ya ce ki taso ki koma bq acan zaki rika kwana” “Idan naje ai Mama Fulani fada zata min” Na fada cikin kuka ina murja idona. “Ba zata miki ba tun da danta ne ya saki, mi akai miki kike kuka?” “Ba komai” Na fada ina turo bakina tare da mikewa tsaye nadauki jakana da plates din da tabarmar da na nade na bi bayan Inteesar, tana gaba ina biye har muka isa wani bangare na can gefen part din Ammy, an zagaye gurin da wani dan karamin gate, ciki muka shiga ni dai ina ta jin tsoro daman can gida mai fadi sosai tsoronsa na ke ji, wasu kanann dakuna na soma hangowa gefen dakunan an kawata su da fulawoyi gwanin sha'awa, da muka isa gurin dakunan sai na tsaya na ki na karasa ciki har sai da Inteesar ta hau saman dan karamin matakalin ta tura kofar daya daga cikin dakunan da suke gurin. “Ke karaso ba komai” Nake kafada nai alamar ni ba zan zo ba, dan ina jin tsoro taya zan iya kwana a nan ni kadai. Dage labulen tai hakan yasa na karasa kusa da ita ina kallon dakin, katuwar katifa ce a kasa an lullube ta da zanen gado mai kyau da filo har biyu a kai, a gefen dakin kuma wata kofa ce wacce nake saka ran bandaki ne a can. “Ki shiga” “Ni ba zan kwana a nan ba” “Ba komai fa kuma kin ga akwai fanka da katifa” “Ni bana so” Ta saki kofar taja kofar ta juyo ni ma na juyo na biyota har sauri nake kar ta barni baya. Muna fito daga bangaren muka hango Aliyu tsaye jikin wata kyakkyawar mota yana kokarin bude ganin mu ya yasa shi tsayawa yana kallonmu. “Ya Aliyu ta ce wai bata so ba zata zauna a can ba” Kallona kawai yai ya dauke kai ya shiga motarsa aka bude masa gate ya fice daga gidan. Ni kuma na koma garejin na shimfida tabarmar ta na aje kayana na kwanta a gurin hankali ya fi natsuwa da nan din duk da a nan ma ina jin tsoro amman gwara nan da can din. Ina kwance na ji ana kira na. “Ataa” Muryar Anty Rukaiya ce hakan yasa ni saurin amsawa na mike da sauri na nufi part din Mama Fulani, a bakin kofar falon na same ta tsaye. “Ance ki je ki gyara part din Ya Muhseen ashe ba ki gyara shi ba ko?” “Wankin da aka saka ni yasa na manta” “To yanzu an tuna miki” Ta fada tana yatsina fuska, sannan ta kauce jikin kofar ni kuma na raba gefe na shiga na dauko tsintsiyar da mopper da robar da nake zuba ruwan mopping din ciki na hada komai sannan na dauko na nufo part dinsa, ina isa bakin kofar na kai hannu na tura kofar falon na shiga na yi zaton ko baya ciki sai na same shi cikin falon a zaune yana video call da wata, ganina yasa ya katse video ya kalle ni fuska a hade wai shi har yanzu fushi yake da ni, yana kallona nai saurin gaisheshi ina risinawa. “Ina wuni” “Ban sani ba, ba na ce karki sake min magana ba?” “Yi hakuri” “Fice ki ba ni guri” “Mama Fulani ce ta na zo na gyara gurin” Na fada ina dan turo baki idona na kokarin cika da hawaye. Maida kansa yai gurin wayar ba tare da ya kula ni ba. “Ya Muhseen kai hakuri ka daina fushi da ni ba zan sake boye maka komai ba daga yanzu” Na fada cikin da damuwar yadda ya ke min tsakanin jiya da yau, domin har ga Allah na damu da rashin kulani da yake yi. Kallona yai sai ya sakar min murmushi. “Na ji” “Na gode” Na fada nima ina murmushi tare da daukar ruwan mopping din ma nufi bedroom dinsa. Shara na fara yi na kawo ta bakin kofar falon sannan na soma mopping, ina cikin mopping din ya zo bakin kofa ya tsaya yana kallona wayarsa a hannunsa. “Pretty karki sake wanka Garden kin ga ke macece ba namiji ba, i'm sorry dazun na kasa dauke idona akanki kina da kyau gaskiya ba zan boye miki ba kina da abun da ake so a jikin mace kin san ni bana gani nai shiru, amman dai karki sake wanka a garden” Kunya ce na ji ta rufe ni, ni har na manta da zancen ya ganni ina wanka dazun amman yanzu ya tuna min sai na ji babu dadi. “Bana son wanka a bandakin mai gadin ne shiyasa” “Be ma dace ki yi wanka a can ba, shi ma ai namiji ne, idan za ki yi wanka ko wani abu ki shiga bangaren Mama ki yi” “Ai kasan Mama Fulani ba zata yarda ba, dukana ma za tai” “To ki shiga bangaren Ammy ko kuma ki zo nan idan ina nan zan fita naje part din Mama Fulani har ki gama, amman karki sake wanka a garden” “Tau” Na fada a ladafce sai yai murmushi. “Good girl” “Aisha.... ” Kamar daga sama na ji kiran da muryar Aliyu, yadda ya kiran sunan sai ka rantse da Allah shi ya rada min shi, juyawa Ya Muhseen yai yana kallonsa ni kuma na saki mopper na nufo kofar dan ganin mai kiran duk kuwa da muryar mai kiran na karantar da cewar a hasale yake. Aliyu ne tsaye a kofar falon fuska a hade. “Fito” Ya fada a tsawace. “Mama fulani ce ta ce na gyara part din Ya Muhseen” “Fito na ce kar na sake ganin kin zo nan” Ta fada da kakkausar murya. “Kamar ya?” Ya Muhseen ya tambaya, sai Aliyu ya watsa nasa harara. “Haka kawai zata zo nan ta kebe da kai da sunan wani sharan daki” ZAKI By Khadeeja Candy 24... Kadan-kadan yake tuka motar yana ta kallo har na soma tsarguwa na takure guri daya, sai yai murmushi ya kai hannunsa ya bude wani dan gurin ya dauko wata yar karamar kwalba mai kamshin gaske ya miko min turare a cikin mai shegen kamshi na kamfanin Awwaba scent ya miko min. “Wannan turaren tun da na siye shi ban yi amfani da shi ba, amman dai kanwata ta fada tace yana da kyau sosai” Ina karbar turaren kamshi ya baibaiye tun kan na bude. “Yana da dadi?” Na gyada masa kai alamar eh sai yai murmushi. “Miyasa baki son yawan magana ne? Ni fa labari na ke son ki ba ni” “Labarin me?” Na tambaya ina dago kai na kalleshi sai ya sakar min murmushi. “Mi ya kawo ki aikin garin Abuja, maman ki ta saka ki?” “Aa ni na saka kaina, bata son zuwan nama ma” “To miyasa kika zo? Kina ganin sha'awar Abuja ne?” “Mutum ya taba sha'awar abunda be taba gani ba?” Ya daga kafadunsa. “Maybe kin san wani idan yana jin labarin gari sai yaji yana sha'awar zuwa wata rana” “Ban taba sha'awa ba, ban taba tunanin zuwa ba, ni da bani da lokacin fira ma wa zai ba ni labarin Abuja?” “Kamar ya kina zuwa makaranta ne acan?” “Aa na yi karatun primary daga bakin class 4 na daina zuwa har yau” Kallon yai da mamaki. “Mi ya hana ki zuwa” “Ba komai” “Ba komai hakan nan kawai zaki ki zuwa makaranta? Ba ki son karatun ne?” “Ina so” Shiru yai ya cigaba da tukin can kuma ya kalleni ina ta wasa da kwalbar turaren daya ba ni ya ce. “Gashin nan na ki na son gyara kin taba gyara shi?” “Eh ina wankewa” “An taba wanke miki a shago?” “Bari na biya da ke shagon da ake wankewa Ilham sai a wanke miki na ki” “Da gaske?” Na fada ina wara ido daman na dade ina sha'awar a wanke min gashi a shago. “Yes yar fara” Ya fada yana dariya ni kuma nai murmushi, ban kara ce masa komai ba shi ma be ce min sai dai ina lura da yadda yake ta kallona har muka isa gaban wani katafaren shago mai hotunan mata da gashi irin nawa su da kitso wasu kuma an gyara musu ya sauko har gadon bayansu. Sai da ya fara fita sannan ya zagayo ya bude min motar na sauko ina rike da turare sai ya mika hannunsa ya karba. “Kawo a aje turare har mu dawo” Ba musu na mika masa sai ya maida kwalbar cikin mota ya rufe motar sannan na nuna min hanyar shagon da hannu. “Muje” Ni ce a gaba shi yana baya har isa bakin kofar shagon, sai ya kai hannu ya bude min kofar na shiga sannan ya shigo shi ma, dukan wadanda suke shagon kabilu ne ba hausawa ba, da yaren turanci yai magana da su sai wata ta zo taja hannuna ta kai ni wani kebantaccen daki mai kamar falo an gyara ko'ina kamar kana gida, kujera ta ja mi na zauna gaban wani katon madubi shi kuma ya zauna a kujerar dake bayana ya dauki magazine yana dubawa. Wani garin tawul ta dauko ta dora min a wuya sannan ta cire dankwalin kaina tana fadin. “Wow.....” Har Kamal ya dago ya kalleni ta cikin madubi ni kuma nai murmushi sai shi ma ya mayar min. Sai da ta fara raba kaina gida hudu ta gyara ko wane bangare sannan ta saka na taso daga wannan kujerar na koma gurin wata na ta shafa mai..... Mun kusan awa daya a shagon sannan aka kammala gyaran gashin, kamar wata ba indiya haka na fito gashin kaina ya kwanta irin yadda na indiyawa yake yi, yana ta sheki ni kaina sai da ya burge balle kuma Kamal da ke ta kallona ba ko kyata ido. Wayarsa ya saka yana ta dauka ta hoto, ita kanta wace ta gyara min gashin sai da ta dauki hoto a wayarta, sannan ya biya kudi muka fito yan matan da ake ma gyaran gashin sai kallon nawa kan suke, domin kowa ya ga nawa gashin yasan cewa nawa ne ba kamar su da ke sakawa fake ba. Wannan karon ma shi ya sake bude min motar na shiga ya rufe sannan ya zagaya ya shiga mazaunin direba ya tashi motar muka hau titi. “Kina da kyau sosai Mamana” Ya fada ba tare daya kalleni ba, ni kuma na kalleshi ban ce komai ba ya maida dubana gurin titin. “Har yanzu baki bani labarin dalilin zuwanki Abuja ba” “Aiki na zo yi" Na fada ina shafa gashin kaina da ke burgeni ina jin kamar ba nawa ba ne. “Mu yan asalin yola ne, fulanin yola ne mu, mahaifina ma'aikacin gobnati ne mai rufin asiri, a hannunsa na taso ina da yayye maza biyu da mace daya ni ne na hudu kuma ima da kanen biyu mata, a unguwar da nake zaune babban yayanmu da Matarsa ne a gidan da kuma Mahaifiyata da kannena sai dai kowa bangarensa dabam, yayana dan majalisa ne a nan Abuja” Na kalleshi. “Ka ce min kai talaka ne ashe ba haka ba ne” “Yes ni talaka ne kamin yanzu, a lokacin da muke yola mun sha wahalar rayuwa, domin mahaifinmu ya rasu a lokacin da muke da bukatarsa, karatu ya so ya lalace sanadin hakan, amman talakawan nan da nake fada min na unguwarmu su suka hada kudi suka komai na makaranta domin suna ganin kimar mahaifina sosai, dattijon arziki haka suke kiranshi, da taimakon da suka min na kawo a inda na ke a yanzu, kin ga ko ai dole na san darajar su” Yana fadar hakan ya faka motarsa gefen titi ya juyo ya kalleni. “Fada min ke fa?” “Ni ba yar kowa ba ce, babana ya rasu ina da kane Lukman shi ma ya rasu, daga ni sai Mamana muka rage” “Ayyah sorry" Ya fada cikin yanayin da ke nuna tsantsar tausayinsa a kaina. “Kika ce ke kika kawo kanki aiki a nan miyasa?”Ban boye masa komai ba face zancen cire kodar mahaifiyata shi ma saboda ina tsoron kar Mama Fulani ta ji ne ta koreni dan sanan ba zata yarda cewar danta ya cirewa mahaifiyata koda ba, sai nai ma Kamal wata karyar da cewar ulcer ce take damun mahaifiyata na ke nema mata kudin magani, tsantsar tausayin da na gani a idon Kamal da fuskarsa ban taba ganinta a fuskar wani mai ganin tausayina kamar haka ba. Da kansa y ciro tissue paper ta gaban motarsa ya miko min. “Share hawayenki” Na karba na share hawayen da suka ki su tsaya min saboda tuna da irin rayuwar da na baro da kuma kalubalen da ke gabana. “Kin yi kokari sosai Ataa kin zama jaruma, aiki a titi kula da mahaifiya ba abu ne mai sauki ba ko a gurin babba balle ke da ba zaki wuce 16 to 17 years ba, amman ina yan uwanki ba ki da kowa wanda zai iya kula da ku bayan rasuwar mahaifinku? Ya kamata ace sun kula da mulallinku ba su bar ku kuna ta bara ba” “Ban san inda kowa nawa yake ba, mahaifina be taba firar kowa da ni ba, haka ma Mamana bata taba fada min wani abu daya shafi danginta ko dangin mahaifina ba, iyakar abunda na sani suna nijar” Ajiyar zuciya ya sauke yana ta kallona sannan ya tashi motar ya hau titi muka cigaba da tafiyar, be sake ce min komai ba sai kallona yake har muka isa gida, a bakin gate din su Mama Fulani ya faka motarsa ya mika hannunsa baya ya dauko ledodin da aka saka masa a bayan mota ya miko min. “Ungo wannan na ki ne” Kin karba nai. “Aa Mama Fulani zata iya min fada idan ta gani?” “Ai ni na baki kuma yanzu da na aje motata a gida zan shigo cikin gidan a nan zan ci abinci rana” Na saka hannu biyu na karba, sai ya saka hannunsa aljihu yan bandir din dari biyu ya miko min. “Ungo wannan ki aje mana, za mu fara tarawa kudin maganin Mama” Kallonsa nai baki a sake sai nai saurin girgiza masa kai. “Aa ba zan karba kudi ba, idan Mama Fulani ta gani dukana za tai kuma aikin da nake saboda na tara kudin na ke za su iya idan na tara na wata uku” “Ba za ki bari ta gani ba ai, boyewa za mu yi ki rika sakawa cikin kayanki, idan mun tara da yawa idan za ki je ganin gida sai a kaita asibitin ko?” “Mama...” “Ya isa, komai dai Mama Fulani zan mata magana ta daina takura miki” “Aa dan Allah ka rufa min asiri wallahi zata iya dukana ma” “To karba ki aje, karki bari ta gani sai ki boye abun ki ai” Babu yadda na iya bayan karba domin ni ma kaina na san ina da bukatar kudin, dan haka na saka hannu biyu na karba cikin tsoro da firgice har na manta ban masa godiya ba, shi ya fara fita cikin motar ya zagaya ya bude min ya fito sannan ya rufe motar, wani abun da ban sani ba ashe Aliyu yana tsaye bakin gate din yana kallonmu amman ni ban lura da shi ba har sai da na ga Kamal yai murmushi ya daga masa hannu. “Sannu dai Aliyu” Sannan na koma cikin motar yaja abarsa zuwa gaban gate din gidansu ya danna horn aka bude masa ya shige ciki. Ina tsaye a inda ya aje ni ina kallon Aliyu da ke tsaye daf da gate din yana watso min wani kallo mai ban tsoro fuskarsa a hade kamar bakin hadari, tsakanin jiya da yau Allah ya saka min tsoronsa duk wani fitsara da nake jin zan iya masa sai na ji yai min kwarjini har na gagara karasa gurin gate din na shiga shi kuma yai tsaye a gurin yana ta kallona kamar daman can dan kallo kawai aka halliccesa. Ganin ba zan zo ba yasa ya juya ya koma cikin gidan, yana wani irin taku na masu karfi da kuzari. Sai na tabbatar ya shige ciki sannan na nufi gate din na tura kofar na shiga, sai na ganshi tsaye da alama ni yake jiran na shigo ni kuma nai tsaye a gurin dayan hannuna da kudin dayan kuma da ledodin. ALIYU POV. Tun ya bar gidan Mama Fulani ya saka samun sukuni da walwala a yadda yake, zuciyarsa na ta raya masa Muhseen zai iya cutar da Ataa, ya san Muhseen ba dan iska ba ne, amman ai ba a shaidun mutum a yanzu, kuma yadda Ataa take da kyau zai iya rudarsa ya jefata cikin wani halin, wanda yake da tabbacin shine silar komai tun da shi ne silar cire kodar mahaifiyarta har ta zo aiki a gidan, idan kuma wani abun ya same ta ai duk shine sila, dan haka ba zai bari rayuwarta ta lalace ba, ba zai taba yarda ta rika kebewa daga ita sai Muhseen ba, daman can tsakanin shi da Muhseen basu taba shan inuwa daya ba, saboda Muhseen yana jin haushin yadda yake da jin da nuna isa da dakama, shi kuma yana jin haushin yadda Muhseen yake da sakewa da mutane. Daga gidan Mama Fulani ya nufo gidansa cikin bacin rai, duk yadda yai kokarin ya kawar kar Rahma ta fahimci yana cikin damuwa sai ya kasa, in every minute sai ya ji kamar wani abun ne zai samu Ataa duk kuwa da yasan be barta mugun guri ba amman ya kasa natsuwa da zamanta a gidan tsakanin jiya zuwa yau. Rahma kallonsa take har ya shigo cikin falon ya karaso kusa da ita ya zauna yana matsa kansa alamar yana masa ciwo. “Lafiya dai, na dauka sai nine zaka dawo gida idan mun ga Doc Perry?” Kissing dinta yai sannan na kwantar da kansa jikin kujerar ya lumshe ido na wani lokacin sai kuma ya ciro wayarsa yai danne danne ya tura mata. A take sakon ya shigo wayarta da sauri ta dauki wayar dake gefenta ta duba. “Za mu iya bari zancen Doc Perry for now? Bana son zuwa gurinsa” Kallonsa tai bayan ta gama karanta sakon. “But why? Wata kila ma mafita ce ta zo mana, waya sani ko waraka ce” Dagowa yai ya zauna daidai yana kallonta. “Rahma akwai abunda ban taba fada miki ba, ban so wannan maganar ta fito daga bakina ba, amman ban san iya lokacin da zan yi ta aje ta ba” Kara matsawa tai kusa da shi da maida hankalinta gurinsa tana kallonsa kunnuwanta cike da kwadayin jin ko mienene daman yau ta fahimci yana cikin damuwa. “Minene Aliyu akwai wata matsala ne? Fada min” Wani dogon numfashi yaja ya sauke ya shafa fuskarsa cikin yanayin da ke nuna yana cikin damuwa, daman kuma a cikinta yake. “Rahma ban sani ba ko zaki fahimta, ban san yadda za ki kalli abun ba, kuma ban san yadda za ki kalleni ba” Saurin kama hannunsa tai. “Fada min kawai Aliyu minene matsalar?” “Rahma duka tsawon lokacin da muka dauka matsalar daga ni ne..” Da sauri ta rufe bakinta sai kuma ta girgiza masa kai hawaye na cika idonta. “Ba daga kai bane Aliyu sun ce ba mu da matsalar komai ba daga kowa ba ne, suna cewa za mu iya haihuwa a duk lokacin da Allah ya kaddara” “Na boye miki ne saboda bana son ki damu, amman maganar gaskiya matsalar daga ni ne, a duk inda muka je ina sakawa likitocin su ce mu duka ne bama da matsala amman serious matsalar daga ni ne” “Aliyu ba haka ba ne... ” Ya rika fuskarta. “Haka ne, kin san ba zan boye miki komai ba, ba zan miki karya ba, be kamata na kyale ki ki yi ta wahala akan abunda daga ni ne ba, na san idan muka je gurin Doc Perry dole zai fadi gaskiya domin shi baya karya” “Duka shekarun nan da muka dauka da gaske matsalar daga kai ne? Ko kuma daga ni ne kake boye min?” “Daga ni ne” Hawaye ne ya sauko mata sai ta kwantar da kanta jikinsa. “Miye amfanin fada min a yanzu Aliyu? Miyasa ba ka cigaba da boyen sirrin ba?” “Saboda bana son ki yi ta wahalar da kanki akan abunda na san ni ne silarsa” Rumgume shi tai ta fashe da kuka. “Ba amfanin bayyanawa Aliyu, kai na ke so ba abunda ban gani ba, jin wannan kuma ba zai hana mu cigaba da neman haihuwar ba, wata kila gaba mu dace ba mu san inda rabo yake ba, da matsalar daga kai ne wata kila zan mu iya dacewa ka samu waraka” Shafa kanta yai yana kara janta a kirjinsa ita kuma ta fashe da kuka mai tsanani har ya rasa ta ita zai fara rarrashinta. A haka suka kwana tana ta kuka, wanda yake tunanin wata kila da yace matsalar daga ita ne wata kila ma ba zata damu kamar yadda ta damu haka ba.“Kamal dai soja abokinka?” Nasir ya fada cikin tsananin mamaki, Aliyu be ce masa komai ba, daman kuma ya san ba zai amsa basa ba, sai dai tunda yaji yai shiru ya san cewar Kamal din ne. “Ina ya hadu da ita?” Nasir ya sake tambaya, sai Aliyu ya fito daga gurin ya nufi kofa rai a bace, cikin sauri Nasir ya ce “Aliyu ina za aka je?” “Na zuba musu ido su lalata mata rayuwa?” “Kana da tabbacin bata nata rayuwa za su yi? Daga Kamal har Muhseen ba irin samarin nan ba ne” “Bana iya shaidar kowa sai kaina, idan ban taka musu burkiba lalata mata rayuwa za su yi, akan mi zai dauke ta ya fita da ita? Waya bashi izinin ma?” “Ai ba yau aka saba ba, dan mace ta kebe da wanda ba muharraminta ba ba wani abun ba ne, naga gidanka ma namiji ne yake muku girki ya gyara gidan” “Nasir baka da hankali kai ma, Rahma ai babba ce ta san ciwon kanta, ba zata bari wani ya yaudareta ba, wannan kuma karamar yarinya ce tunaninta be kai can ba” Yana fadar hakan ya saka katinsa kofar ta bude masa ta fice. Nasir ya bishi da kallo yana murmushi. “Aliyu kenan, at least dai yarinyar nan ta sa ka fara motsi kamar na miji, sai yanzu kasan da muharramin?” Ya fada yana cigaba da murmushin tare da zaunawa saman kujera ya cigaba da aikinsa. Kai tsaye gida ya nufa gudu yake amman yana jin tafiyar ta masa nisa yau, a kada horn daya yake danna amman daya bisa bakin gate din sai da ya danna horn ya fi hudu a lokaci daya, har mai gadi sai da ya ji tsoro yai tunanin ko wani abun ne ya faru. Daf da kofar falon ya faka motarsa ya fito cikin zafin ran da be san ta ina yake fito masa ba ya shiga cikin falon ba ko sallama, Rukaiya ya samu kwance a kujerar tana lasar waya tana dariya da alama chat din ya mata dadi. “Ke ina Ataa” A firgice ta tashi zaune domin hankalinta yana kan wayar bata ma san da shigowarsa ba. “Na'am tana, tare muka fita shopping shine sai Kamal ya ce na bashi aron ta ta taya shi shopping idan suka gama zai kawo ta gida” “You're very stupid” Ya fada yana kara matsawa kusa da ita cikin wani irin yanayin bacin rai marar misaltuwa, tana ganin hakan ta tashi da gudu ta nufi upstairs tana kiran sunan Mama Fulani, ta san baya dukansu ko ba su ba abu ne mai wahala ya saka hannunsa ya daki mace amman a yadda ta ga bacin rai a fuskarsa a yau ta san komai zai iya faruwa. Da sauri Mama Fulani ta fito daga dakinta dankwalinta a hannu yana tambayar ba'asi. Cikin kuka Rukaiya ke fada mata abunda ya faru sai ta nufi downstairs tana kallon Aliyu tare da fadin. “Ta fada min ai, Kamal ne ya ce a ara masa ita” “Ya za ara masa ita kamar wata sutura, idan wani abun ya same ta fa? And you.... ” Ya fada yana nuna Rukaiya sai kuma ya juya ya fice sai huci yake kamar wanda yai gudun ceton rai. Mama Fulani ta saki baki tana kallon ikon Allah. “Wannan yarinyar ta zama fitini ta zo ta koma garinsu ba zata zauna a gidan nan ba, gaba daya Aliyu ya canja ganin yarinyar nan, shi da babu ruwansa da kula da mace? Ji abunda yake?” “Ba sai an koreta ba Mama, Wallahi kamaninta za mu canja, kyau ne yake rudarsu” Maryam ta fada daga can upstairs din da take tsaye. Gate din Aliyu ya nufo ya tsaya yana ta jin kamar ya kira Kamal a waya sai kuma wata zuciyar ta hana shi, yana tsaye a gurin sai ga Motar Kamal ta karyo kwanar yana ta kallonsa har ya karaso kusa da su sai dai ba sosai ba, ya faka motar, sai kuma yaga yana magana da Ataa a cikin motar baya iya jin abunda yake cewa, amman wani irin abun yake ji yana masa yawo a cikin jinin, ji yake kamar ana tafasa hanjin cikinsa komai na jikinsa rawa yake har gumi ke karyo masa a take idonsa suka canja kala, bacin rai ya bayyana karara a fuskarsa, wani abu yaji yana masa yawo a zuciya wanda be taba jin irinsa a rayuwarsa, har numfashinsa na fita da karfi wani na tura wani, ji yake kamar yaje ya bude motar ya fito da Kamal ya shake shi a gurin, sai kuma wata zuciyar ta hana shi, lokacin da Kamal ya fito motar ya budewa Ataa ta fito ya daga masa hannu yana masa sannu ji yai kamar ua narke a gurin saboda zafin rai da wani bakim haushi daya kama shi. Bayan Kamal ya wuce Ataa ne ta gagara shigowa gidan sai ya juya ya koma ciki ya tsaya, sai gata ta shigo hannunta rike da kudi dayan hannunta da ledodi gashin kanta ya kwanta luf kana ganinsa kasan ya sha gyara gwanin sha'awa. Be san lokacin daya isa gabanta ya kware mata ido. “Ina kika fito?” Ya tambaya muryarsa har rawa take. “Kamal ne ya are ni” Ta fada tana turo baki. Hannu yasa ya fisge ledar hannunta da kudin ya bude gate din ya fice ita kuma ta fashe da kuka ta durkushe a gurin. Kai tsaye ya tsallaka titi ya tura gate din gidansu Kamal ya shiga, kadan suka kusa yim karo da juna domin Kamal din ma ya nufo gate, sai Aliyu ya jefa masa ledar da kudin. “Kar ka sake daukar ta ku fita, har ka bata kudi, ba irin yan matan Abuja ba ne, ka je can ka nemi sa'ar ka wannan aiki ta zo ba shashanci ba” Da mugun mamaki Kamal yake kallon Aliyu yana karantar abunda ke zuciyarsa da kuma mamakin bacin ransa akan ya fita da ita har yana fada masa abunda be taba ba ko da wasa. “Fita kawai nai da ita” Aliyu ya nuna shi da yatsa. “Na fada maka ba irin yan matanka ba ne, wannan na zama na farko kuma na karshe” Aliyu na fadar hakan ya juya, sai Kamal yai murmushi. “Zai zama na farko amman ba na karshe ba, miye naka a cikin dan na fita da ita? Kaji haushi ne?” Aliyu ya tsaya cak kamin ya juyo yana masa wani kallon wulakanci. “Abun kunya ne ma ace ka fita da yar aikin gidanmu, har ka kaita saloon a gyara mata gashi what a shame” Kamal yai murmushi ya matso kusa da shi. “Abun kunya ne dai kai a ganka kana fada kan yar aikin gidanku! Ni daman ai nasan daraja talaka ba kamar kai ba, miyasa kake fada akan na fita da ita?” “Ba zan taba barinka ka lalata mata rayuwa ba” “Na lalata mata rayuwa? Like seriously?” Kamal ya fada yana dariya. Harara kawai Aliyu ya watsa masa ba tare da ya sake cewa komai ba ya juya dan ya fahimci bata lokacinsa kawai zai yi a nan. “A da bana son ta kawai burgeni take, amman wannan abun da kai sai ya saka min son ta Wallahi” Kamal ya fada yana bin Aliyu da kallon haushi. Aliyu be juyo ba har ya fice daga gidan cikin zafin rai yana tauna hakoransa har suna kara.. ZAKI By Khadeeja Candy 25... A gurin tunda bachi yai gaba da ni ban sake sanin inda nake ba sai kusan magariba, domin na farka ne a lokacin da ake daf da gabatar da sallah magariba, da sauri na sauka saman katifar naje Garden da katuwar rigata da tai min yawa nai alwala na dawo nan sai na rasa hijab din da zan dauka na saka nai sallah domin komai nawa na cikin jakar ya jike shakaf sai kawai na zauna a gurin na rumgume hannayena ina kallon kasa, ji nai an jefo min abu wanda hakan tasa ni zabura na tashi tsaye da sauri, Aliyu ne ya jefo mij Hijab hannunsa a jike da alama alwala yai shi ma, ban ce masa komai ba na dauki katon Hijab din na zuba na soma rama sallah la'asar sannan na gabatar da magariba. Bayan sallah isha'i Muhseen ya bude kofar ya shigo daure da plate din abinci da ruwa a kofin ruwa ya dire min a gabana, tuwon shimkafa ne miyar ganye da tea mai zafi a kofin. “tashi ki ci abinci” Na tashi ina ta leken kofar daya fito. “Idan Mama Fulani ta gani zata maka fada” Murmushi kawai yai ya matsar min da plate din. “Bana son tuwon” “To ga Tea Ya dauki kofin ya mika min, ni kuma na karba na kai a bakina, ina cikin sha Mama Fulani ta shigo ta kofar gaba sai nai saurin aje kofin na mike tsaye shi ma ya mike tsaye yana kallona da mamaki kamar be ga mahaifiyarsa. “Muhseen ban ce karka sake shiga zabgar yarinyar nan ba? Ban isa da kai ba ne” “Haba Mama wane irin ba ki isa da ni ba kuma? Amman zancen na fita hanyarta be taso ba, haba Mama ke ma ai ya kamata ki fahimci wani abu” “Na gane me? Muhseen kana da hankali kuwa? Kasan abunda kake yi? Abun kunya kake son ka dauko mana? Yar aikin gidanku? Ai ko ganin ka akai kana mata magana abun kunya Wallahi a garemu kaskantacciyar yarinya kamar wannan?” Shiru yai ba ce komai ba sai ta juya ta fice daga gurin, ni kuma na koma na zauna na kasa sanye tea din. “Kar abunda Mama tace ya dame ki haka take wani lokacin idan ranta ya bace, shanye ki ba ni kofin” Daga idona nai na kalleshi. “Idan kana min abunda Mama Fulani bata so, zan ka iya samu matsala da ita, kuma ni ma zaka ja min wata matsalar, wata kila ta koreni ko ta dake ko wani abun dabam” Lankwashe kafafunsa yai ya zauna gabana yana kallona tare da soma min magana a hankali. “Ban taba zabar abokin rayuwa a wajen mu'amala ta abota ko ta aiki ko wani abun ba, ban taba gabatar da wata mace a matsayin wacce na ke so ba, duk da kasancewar akwai matan da zan gani na ji sun kwanta ko kuma su nuna ra'ayinsu a kaina, a talaka da mai kudi duka daya ne a gurina, domin duka mutane na dauke su, banbanci kawai su suna da kudi mu kuma bama da su, abota da talaka ko auren talaka ko zama da talaka ba zai taba damuna ba, matukar ni zuciyata ta kwanta da mutumen” Shiru yai yana murmushi sannan ya cigaba “Mama tana da wani hali da ni kaina bana son shi, ni kaina bana son irin rayuwar da take na kin jinin talaka, dana daya daga cikin dalilin daya saka ba mu jituwa da Aliyu, ita kanta Mama ta fin jin natsuwa da Aliyu fiye da ni, domin be rago komai a halinta da yanayin rayuwarta ba, har mamakin mu ke yadda ke yau ya sassauta miki ya doki Maryam saboda abunda tai miki, bayan be taba saka hannunsa ya dake kowa a gidan nan ba, sai da na fi alakanta hakan da zalincin da Maryan tai miki, domin baya son ya zalinci wani ko ya ga an zalince, sai dai fa ba shi da mutunci kuma hakan ba zai saka ya sake maka ba” Hannunsa ya kai ya kama hannuna. “Wata kila da ke zan iya canja musu rayuwa, wata kila da ke zai saka Mama ta fara daukar talaka da daraja, wata kila da ke Aliyu zai zubar da wannan halin nasa na nunanin talaka ba komai ba ne, kina da abubuwan da ke so a jikin mace, fari kyau gashi kurciya hankali ladabi da kuma kuzarin aiki, kin kwanta min sosai a raina Ataa tun ranar dana fara ganinki, dan talauci ba zai saka na kyamace ki ba, ko na kasa nuna kaunata a gareki ba, wata kila idan kika shigo cikinmu Rukaiya Baby Maryam Ahmad Aliyu Mama da duk wani wanda baya ganin darajar talaka zai daina ko ya rage, idan na samu sa'a kika so ni....” Be karasa ba nai saurin fisge hannuna ina kallon cikin idonsa da mugun tsoro, ba tsoro na a dake ni ko amin wani abu ba, tsoro na kalamin daya fito daga bakinsa ji nai kamar kunnuwana ba za su iya dauka ba, kalmar ki so sai ta shiga a zuciyata tai min fadi sosai har ta sakar min nauyi a kirji. “Kwantawa zan yi” Na fada muryata na gargada a take na soma jin zazzabi na dawo min, be sae ce min komai ba, bayan yawun bakinsa daya hade ya dauki plate din da cup ya fice. Da sauri na kwanta saboda nauyi da naji kirjina yayi na kife ina ina fitar da numfashi daker, wani be taba fada min magana mai nauyi kamar wannan ba, a cikin talakawan yan'uwana babu wanda ya taba fada min haka, ban taba kawo wa raina wani zai so ni ba, shiyasa ni ma ban taba jin son kowa a cikin raina ba. “Idan na samu sa'a ki ka so ni....” Kalmar tana ta maimaita kanta ta cikin kunnuwana, a take na fashe da kuka ina jin wani sabon al-amari da ban taba ji ba, kuka na rika yi sosai kamar wacce aka daka ko aka fadawa wata bakar magana, sai na ji ina da bukatar mahaifiyata a kusa da ni ji nai kamar ace Nana tana kusa da ni na rumgumeta ta rarrashe ni amman ba dama. ALIYU POV. Sai da yai sallah magariba a unguwar sannan ya isa gida yana ta jin babu dadi a abunda Maryam tai ma Ataa and ganin Muhseen na bata magani ma it pain him domin yana ganin kamar cutar da ita kawai Muhseen zai yi, yana da tabbaci zai iya kare kansa daga duk wani abu da zai kusantar da shi daga Zina amman ba shi tabbaci wani zai iya kare kansa daga hadawa hallakar zina, ba kuma duk wannan yake damunsa ba, babban damuwarsa zuwan Ataa gidan saboda nemawa mahaifiyarta maganin kodar da aka cire mata wanda shi ne sanadi duk da ba da saninsa da amincewarsa aka cire ba, yanzu kuma idan wani abun ya same ta ai duk saboda shi ne. Babban plan din da ke gabansa na ya taimaki mahaifiyar Ataa ne ya nema mata magani ta samu lafiya sannan ya nemi yafiyarsu wata kila zasu yafe masa, amman ya kasa tunkarar Ataa kai tsaye da hakan, saboda tana fada masa magana son ransa a duk lokacin da yai maganar mahaifiyarta shi kuma girma kai da jin kai ba zai barshi ya iya tsayawa ya fahimtar da ita ba. Horn daya yai aka bude masa gate ya shiga cikin gidan ya faka motarsa a inda ya saba fakawa, sannan ya bude motar ya fito ya nufi kofar shiga falon, wutar falon a kunne take sai dai tv a kashe kamar yadda ya fita ya barshi amman ya an gyara komai na falon wanda hakan ke nufin mai gyara gidan ya zo ya gyara ya tafi, dakin Rahma ya fara nufa ya tura ya shiga, sai ya same ta kasa kwance ta dafe cikinta zuwa awanzunta tana wani irin daukar rai kamar zata mutu, wayarta na nesa da ita a kasa, da alama kubucewa tai a hannunta ta fadi kasa, hawaye na ta fita a idonta. A firgice ya karasa kusa da ita ya rikota yana taba fuskarta. “Rahma minene?” Kasa magana tai sai ta bude baki tana fitar da numfashi daker, da sauri ya dauke ta ya fito da ita ya saka a mota kamin ya shiga motar ya kwalawa mai gadin kira ya ce ya bude masa gate, @360 ya fisgi motar ya fita daga gidan ya dauki hanyar babban asibiti, kamin ya isa hankalinsa ya tashi sosai yana ta ganin kamar Rahma mutuwa zatai a motar, sai duk yaji tafiyar ta masa tsawo yana jin kamar ana mayarda shi baya. Yana isa emergency aka karbe ta kasancewar asibitin ta manyan masu kudi ce ga kayan aiki a take aka hau bata taimakon gaggawa, shi kuma ya kasa tsaye ya kasa zauna sai da ya ga an fito da ita daga dakin an kaita wani dakin an saka mata oxygen an saka mata wata allura a hannu, komai likitocin ne suka mata ba kamar nan da ake cewa mutum ya dauki mai jinya yaje ya kaishi a masa hoto ba, su da kansu suka dorata a wani gado suka kaita wani dakin aka dauki hoton jikinta gaba daya sannan aka dawo da ita wani likitan ya shigo ya debi jininta ya fita. A lokacin ne Aliyu ya samu natsuwa har ya kira Mama Fulani da Ammy da kuma Momy ya fada musu kamin ya kira familyn Rahma su ma ya fada musu. Zauna yai kusa da ita ya kai hannunsa yana shafa fuskarta dayan hannunsa kuma cikin hannunta yana murzawa a hankali, kallo daya zaka masa kasan yana cikin tashin hankali rudani da tsoro a lokaci daya. Ba ayi minti talatin ba sai ga Mama Fulani da Ammy a asibitin sun zo, hankalin Mama Fulani ya fi tashi fiye da na Ammy ita kuma ba dan Rahma ba sai dan Aliyu da ta san zai tashi hankalinsa saboda Rahma, domin shi Mama Fulani take kallo ba Rahma ba. “Jiki ai da sauki” Mama Fulani ta fada. “Eh da sauki gaskiya tun da yanzu sun saka mata oxygen zata samu saukin numfashin, kuma sun mata hoto ko minene za su ga ni ai” Ammy ta ce. “To wai miya faru ne da ita?” “Wallahi ban sani ba, ina komawa gida na same ta a dakinta kwance kasa ta dafe cikin tana daukar numfashi” “Allah ya sauwake" “Amin” Ya amsa yana picking din calling don da Mommyn Rahma ke masa, cikin sautin kuka ta ce. “Fada min addreshin asibitin ga kanwata nan da take Abuja zata zo ta duba mana jikinta” “Jiki da sauki fa ta samu bachi ma” Haka ya fada sannan ya fada mata inda asibitin take ya kashe wayar, sai ga wani likita ya shigo ya ce duk su fita basa son ganin kowa akan marar lafiyar, daman a ka'idar asibitin ba a aje mai jin marar lafiya su suke masa komai ba a kwana a asibitin da sunan jinya suna da nurses da suke kula da marar lafiya da ko mai jinyar ba zai iya kula da shi haka ba. Gaba daya suka fito daga dakin suka bi bayan baturen likitan zuwa office dinsa domin ya fada musu yana son magana da iyayenta ko mijinta, a lokacin da suka shiga office din sai suka samu ba likita daya ne a ciki ba, likita biyu suka tarar yan Nigeria bayan wannan baturen da suka shigo tare da shi, a bayan teburin likitocin an laka wani katon majigi mai kamar kwanfuta an laka wasu hotuna a jikin abun. A visitors chairs suka zauna shi kuma likitan ya nufi inda computer take ya cire hotunan jiki ya dauko wasu ya laka da wani dan pen na hannunsa ya nuna musu inda matsalar Rahma take yana musu bayani da halshen nasara. A bayanin da likitan yai da wanda sauran likitocin sukai babu wanda Aliyu ya fahimta, ba dan baya jin turancin ba, sai dan jin abun wani banbara gwai, wai kodarta ta kone as how kodar mutum zata kone? Ba ma lalacewa ba? And duk duka yaushe aka saka mata kodar da za a ce ta kone? Gaba daya rikecewa yai ya tashi ta sauri ya fice daga office din ba tare da ya jira likitan ya gama bayanin ba. Ammy ba ta wani dade asibitin ba bayan likitan ya gama musu bayani suka fito suka samu Aliyu tsaye a waje duk ya bi ya rike kamar ba shi ba, shi kansa ya san Allah kadai ya iya haka, ace koda ta kone, gashi kodar ce daya ta rage mata wacce aka dasa mata sai kuma ace ta kone, kamin ma ya samu wata aiki ne, and ba zai zama ace ko da yaushe sai an dasa nata koda ba idan an samu wata rana ba za a samu ba. Mama Fulani ce ta tsaya da shi tana ta bashi magana tana kokarin kwantar masa da hankali, har wata kanwar mahaifiyar Rahma ta shigo taje ta duba, yasan dokar asibiti ba a kwana da sunan jinya amman a haka ya karya dokar ya zauna a kujerar ya saka matarsa a gaba yana ta kallonta hannunsa cikin nata, ji yake kamar ya cire ta mata ciwon a take ta tashi, jikinsa nata raya masa mutuwa za tai ta bar shi, and all what he was thinking idan ta mutu ba zai iya rayuwa ba, taya ma zai rayu babu Rahma? Haka ya saka ta a gaba yana ta kallo, misalin 12 ya aikawa Nasir da sakon abunda yake faruwa, da Nasir ya kira shi kuma sai ya kasa dauka, sai kallon wayar yake gaba daya ya rike ce ya rasa inda zai saka kansa, gaba ya saka ta yana ta kallo har garin Allah ya waye, bachi be leka idonsa ba ko da wasa. A wani masallaci dake nesa da asibitin yai sallah asuba gaba daya addu'arsa Rahma yai ma, daya fito daga masallacin sai ya zauna cikin motar ya kifa kansa jikin sitarin motar yana ta sauke ajiyar zuciya idonsa na masa mugun nauyi. kiran Nasir ne ya shigo wayarsa amman ya kasa picking har tai ringing ta katse aka sake kira, gaba daya kasala yake ji yana jin shi ma kamar ba shi da lafiyar. Sako ya turawa Nasir na addireshin inda yake, sannan na kwantar da kujerar ya lumshe idonsa, cikin mintunan da ba su fi ashirin ba Nasir ya iso gurin, babban masallaci ne amman hakan bw hana shi gane motar Aliyu ba, domin irin ta bata da yawa a garin Abuja. Yana bude motar Aliyu ya bude idonsa da suka kada sukai ja yana kallonsa. “Ya jikin nata?” Aliyu yai shiru be ce komai ba sa yawo yake da idonsa kamar marar gaskiya. Nasir ya dafa shi. “Aliyu ka kwantar da hankalinka...” “Wane irin na kwantar da hankalina? Kodar ta fa aka ce ta kone, ko baka gane ba?” “Na gane, amman me likitocin suka ce?” Aliyu be ce masa komai ba, ya jinginar da kansa jikin sitarin yana sauke ajiyar zuciya. Can kuma ya dago ya kalli Nasir. “Saboda kodar nan ta zalinci ce ko? Shiyasa ta kone? Ko kuma saboda Ataa ta ce ba zata taba amfanar Rahma ba? Ta mana Allah ya isa fa” “Gaskiya ne Aliyu zalinci kawai ba ban da addu'ar da tai muku ta isa ta saka wani abu ya faru, domin ita wacan da aka cirewa ba mu san halin da take ciki ba....” “What if na bata hakuri?” Nasir yai saurin tarar numfashinsa. “Karka tinkareta kai tsaye yanzu tun tuni ya kamata kai wannan kuma ba kai ba” “No baka san yadda nake ji ba ne a yanzu Nasir, bana son na rasa Rahma” “Ai ba cewa akai zaka rasa ta ba, amma ...” “No hakuri zan bata Nasir” Ya fada yana jan murfin motarsa ya rufe. Cikin saurin Nasir ya nufi tashi motar ya shiga ya bi bayan Aliyu. ATAA POV. Na tashi da safe da zazzabi da kuma rashin kuzari, dukan abunda ya faru jiya sai ya zame min kamar mafarki ciki kuwa har da maganar da Muhseen yai min. Bayan na gabatar da sallah asuba na dauki jakata na nufi garden na shanya duka kayana da suka jike sannan na shiga part din Mama Fulani na fara gyara falon, na nufi dakin Ammy na gyara mata nata falon, ina cikin saka air freshener na ji tana fadin “Jiya ba ki dawo karbar abincin dare ba, ko da mun fita asibiti amman ni da wuri na dawo saboda Alhaji” Abubuwa ne suka zo min a rai, zancen Alhaji na san tana da mijin da suke taraiya ita da Mama Fulani domin wani lokacin ina ganin yadda suke kokarin shirya abincin ko wani abunda ya ke nuna mijinsu suke yi ma amman ban taba jin zancensa a bakinsu ba, haka ma a gurin yayansa, ban taba cin karo da shi ba, fitar da shigowarshi duka ban taba gani ba, da wace motar yake fita ko yake shigo cikin gidan ban taba sani ba. Sai kuma zancen zuwa asibiti waye ba lafiya? Kamar ta san abunda na ke sakawa a raina sai na ji ta ce. “Matar Aliyu ciwon ya tashi Wallahi” Da sauri na kalleta. “Miya ke damunta?” “Wai ciwon koda ne daman tun tana karama haka take har ta girma, to sai daga bayan kododin duka biyu suka lalace, daker aka samu wata aka siya aka saka mata a waje, yanzu kuma wai kodar ta kone, Wallahi ni yarinyar har tausayi take ba ni wannan jarabawar rayuwa” Wani yanayin na ji, shi ba dadi ba shi kuma na bakinciki ba, a take na girmama Allah a zuciyata lallai sakamakon zalinci ba mai kyau ba ne, koda ta kone abunda ban taba ji ba, sai dai na ji ance ta lalace amman wani iko na Allah yau na ji ance ta kone, lallai Allah ba azzalumin kowa ba ne. “Lafiya?” Ta tambaya ashe kallonta nake ta yi tun dazu ni ban ma sani ba. Har na bude baki nai magana sai muka ga an turo kofar falon an shigo, Kamal ne fuskarsa dauke da murmushi yana sanye da uniform din sojoji sun matukar karbarsa abun ka da dogon mutum sai yai kyau da kakin kamar yadda na ganshi a wacan karon. Ledar jiya ce a hannunsa kai tsaye ya nufo inda nake yana gaisawa da Ammy da alama ya saba shigowa gidan, domin ita ma naji tana masa korafin ya daina zuwa kwana biyu kamar yadda Mama Fulani ma na ji tana masa. “Wallahi aiki ne yai min yawa, yanzu ma kaduna zan je da safen nan sakon kawai zan bawa ba Mamar nan taki” Kallonsa kawai Ammy take har ya karaso kusa da ni ya mika min ledar. “Ga kayanki nan” Tsayawa nai kallon ledar kamar mai shawarar karba, sai ya aje min ita kasa yana kallon agogon hannunsa. “Zaki bata min lokaci ko? Na shiga can a aka ce kina nan” Juyawa yai ya nufi kofa yana yi ma Ammy sallama da kallo na bishi har ya fice sannan Ammy ta kalleni tana dariya ta ce “Ina kika san Kamal?” “Ranar na fit gate shine ya kira na ce masa nan nake, sai kuma da muka fita da Anty Rukaiya shine ya ce na raka shi mu yi siyayya” “Ok shine ya kawo miki na ki tsara? Tooo lallai yarinyar nan ashe ko ko zai janyo miki rigimar Maryam, saurayinta ne fa” Na wara ido. “Da gaske?” “Eh yana dan zuwa gurinta can ba a rasa ba, yau kuma ya dawo gurinki? Oh Maza akwai iya son mata” Ta fada tana dariya ni kuma na nufi inda na dauko turaren na aje sannan na dawo na duka na dauki ledar na fito daga part din na nufo gareji ban tsaya duba komai ba aje kawai nai na dawo part din Mama Fulani dan karasa gyaran kamar yadda na saba, ko da na shiga ita da yayanta suna dinning suna karyawa, fuskar Anty Maryam ta kumbura sosai har gurin idonta daya ya rufe bata iya gani da kyau da shi, wata kila marinta Aliyu yai ta yi ko kuma wani abun ya buga mata a fuska oho, ni dai kallo daya nai mata na dauke kaina na shiga dakunansu na gyara ko'ina na wanke bandakunan sannan saka turare Awwaba na fito na sauko kasa. “Zo ga abincinki ki dauka” Ya Muhseen ya fada yana aje min plate din a gefen taburin. Sai da na karasa kusa da shi sannan ya kalleni “Ya jikinki? Na manta jiya ban saka miki kada ba amman ai baya jini ko?” “Eh ba ya yi” Na amsa shi jikina nata rawa domin na lura da yadda Mama Fulani take watsawa Muhseen harara shi kuma be ma gani ba, gaba daya hankalinsa yana gurina, da sauri na karbi abinci naje na zube a plate dina na kawo masa sannan na dawo garejin na zauna ina cin abincin ina duba kayan da ke ledar, kayan da ya siya min ne jaya turare da auduwar mata da man goge baki sai kuma chocolate da biscuit mai madara. Ina jin lokacin da motoci har biyu suka tsaya a harabar gidan, ni dai ban leko ba domin ban damu na san ko suwaye suka zo ba, a cikin jaka ta na saka man goge bakin da sauran kayan biscuit din kuma na aje shi a saman katifa ta da zimmar idan na dawo na ci, sai na dauki plate din da cup na nufi garden dan wankewa, ina cikin wakewa na ji kamshin turaren Aliyu da sauri na waigo sai na ganshi tsaye yana ta kallona cikin yanayin da ke nuna yana cikin tsananin damuwa. Ni ma tsayen nai ina ta jiran na ji idan wani abun zai ce min amman be ce komai ba, ganin hakan yasa na juya na cigaba da wanke plate din sai na ji motsinsa a bayana daf da ni. Mikewa nai tsaye ina kallonsa, sai ya bude ba ki kamar zai yi magana sai kuma ya kasa cewa komai. Daukar plate din nai zan wuce sai ya kira sunana. “Ataa... ” Sai na tsaya a tunanina wani abun zai ce na masa, sai kuma yai shiru be ce komai ba ya kawarda fuskarsa yana hade yawu, da alama wasu kalmomin yake hadawa ko kuma yana saka abunda zai ce min ne. “Matata Rahma bata da lafiya.... ” Sai kuma yai shiru ya dawo da dubansa a kaina. “Ataa na san ba a kyauta miki ba am.... ” “Sai yanzu ka sani? Saboda kodar matarka ta kone ko? So kake a sake cire ta mahaifiya a saka mata?” Ya girgiza min kai alamar aa. “So na ke na baki hakuri” “Kana tunanin Hakuri zai canja zalincin da aka min ne? Kana tunanin hakuri zai saka Rahma ta tashi a take ne? Ko kuma kana tsoro kar matarka ta tafi ta barka ne ka dandana zafin rashi kamar yadda na dandana na rashin dan'uwana saboda kai? Ko tsoron jinya kake kamar yadda nai ta mahaifiyata? Har ka fara tsorata da abunda ya samu matarka tun yanzu? Likitoci sun fada maka zata rayu ko ba zata rayu ba? Ai kana da kudi sai mu gani idan kudinka za su tare mata mutuwa, ko kuma za su sama mata lafiya a take, ko da yake za ku iya neman wani talakan marar gata irina ku cire masa kodar ku saka mata ita ta rayu” Duk abunda na ke fada masa be ce min komai ba, wani abun mamaki sai ma cika da idonsa sukai da kwalla. Wani mutum ne ya shigo garden din wanda ba zai wuce sa'ar Aliyu ba ya karaso kusa da inda muke tsaye yana ta kallo. “Ke ce Ataa?” Na kalleshi “Wani ya baka labarina ne?” Sai ya kalli Aliyu ya sake kallona. “Sunana Nasir ni abokin Aliyu ne kuma Aliyu ya fada min komai akanki, Ataa mun san an zalince amman....” “Amman me? Amman ba ku gane ba sai yanzu? Ya kasa jure abunda ya same shi ko? Ni na jure jinyar mahaifyarta da kallon halin da take ciki har na tsawon wata daya da wani abu a asibiti, kullum ina ta zullumi zata mutu ko ta rayu? Ban sani ba, yanzu haka mahaifiyata tana can gida na baro ta na zo nan aiki saboda na sama mata kudin magani, wata kila ko da zan koma ta mutu, ko kuma rashin lafiyar ta kara tsanani, tun da na baro garin ban sake jin muryarta sai dai idan na kwanta nai mafarkinta? Saboda abunda mutanen nan suka min, har yau bata san cewa an cire mata koda ba, da wane ido zan kalleta na fada mata? Su wa zan ce suka cire mata? Har yau mahaifiyata bata san gaskiyar ciwonta ba bata san komai a kai ba, kun jefa rayuwata cikin damuwa da bakinciki, amman duk ba ku gane ba sai yanzu da Allah ya jarraba Rahma na dan lokaci, sai ka kasa jurewa? Miye amfanin zuwa da kukai a nan? Na yafe muku? Ko kuma na fada muku Rahma ba Zata mutu ba? Kun cutar da ni Wallahi babu wani dadi bakin da za ku min na yarda da ku, za ku iya cilata ni yin komai saboda ina talaka amman ban da yafiya, ba zan taba yafewa ba.... ” Na karasa cikin kukan dana fara tun dazu sannan na nufi hanyar fita dGa garden din har bana iya gani da kyau saboda hawayen da suke min zuba. ZAKI By Khadeeja Candy 26... Duk kokarin Kamal na rike ta kar ta kai kasa be saka ya iya taro ta ba har sai da ta kai kasan, be san abunda ya faru ba amman tabbas ya ji karan mari a lokacin da ya kawo bakin kofar falon da zimmar shigowa kawo ma Ataa tsarabarta. Gaba daya falon yai tsif Husnat da Siyama suna ta mamakin zafin rai irin na Fulani, Maryam da Rukaiya kam abun dadi yai musu daman ko su ne za su iya yi mata haka, sai dai suna tsiron kar Aliyu yai musu ba dadi amman idan Mama Fulani ce babu abunda zai yi. Momy ta girgiza kai tana kallon Ataa cike da tausayawa domin ta san ba lallai sai ta yi ma Mama Fulani wani babban abu zata yi mata irin wannan dukan ba, tasan halinta sarai tana da zafin hannu a wajen yayan wasu ban da yayanta, ita kam nata yayan baka isa ko yatsa ka nuna musu ba balle ka ce za ka dake su. “Mi tai miki kika mata wannan irin marin? Ta suma fa” Jin hakan yasa Kamal ya dago daga kokarin rika Ataa da yake ya kalli Mama Fulani cikin bacin rai. “Ba lallai sai ta yi mata wani abu ba, ai zalinci ne zata iya dukanta tun da ba Maryam ba ce ko Rukaiya, waya isa ya taba Baby ma da take karama a cikin yayanki amman kin iya duka wata saboda ba ke kika haife ta ba” Da mugun mamaki Mama Fulani da Rukaiya kai har Momy suke kallon Kamal jin abunda ya fito daga bakinsa, Mama Fulani ta nuna kanta tana kallon Kamal “Kamal ni kake fadawa wannan maganar? Ni Fulani?” “An fada miki ko nima dukana za ki yi?” “Kai Kamal karka kuskura ka ce...” Maryam bata karasa ba ya daga mata hannu yana daka matsa tsawa. “Yi min shiru shashashar yarinya, ba ku iya komai ba sai bakin girman kai da zalinci haka kawai ku saka karamar yarinya a gaba kuna azzabtar da ita saboda kawai tana karkashinku, babu wanda zai baro iyayensa ya zo karkashin wani ya tare yana musu aiki sai da babban dalili ba ku san abunda ya rabota da iyayenta ba amman kun saka ta gaba kuna mata wulakanci kala kala son ranku, ku ku yi mata mahaifiyarku tai mata arziki hauka ne? Shikenan ku mutum idan ba shi da kudi ba shi da daraja a gurinku? Wannan wace irin rayuwa ce?” Momy ta ce. “Kamal be dace ka shigo har cikin gidansu abokin ka ba ka fadawa mahafiyarsa irin wadannan kalaman sam be da ce ba” Kamal ya kalleta “Ko ke kikai ba daidai ba dole na fada miki gaskiya balle kuma ita da ba haihuwarsa tai ba, sai mummunar akida da ta saka masa na rashin ganin kan kowa da gashi” “Yar aikin mu ce dan haka duk yadda muka ga dama haka za mu yi da ita, babu uban da ya isa ya hana idan kuma a akwai sai yai na gani, ai ban san ka isa da ita ba har sai ka dauke ta daga gidan nan ko kuma ka rama mata marin da aka mata, sai na san na isa da ita ko kuma na san zumuncin uwa kuka hada ko na uba” Cewar Rukaiya tana wani irin marmadi kamar zata matsa kusa da shi ta dake shi. “Zumunci musulunci muka hada wanda ya fi na jini, kuma zan nuna miki na isa da ita, kuma zan nuna miki ita ma tana da gata kamar ke” “Ba dai kamar ni ba Wallahi, karyar makaskanciya irinta Wallahi abun kunya kana son yar aikin gidan abokinka kuma budurwarka tirr Wallahi” “Ke ce makaskanciya ke da baki san darajar dan adam ba, kuma ni ban taba cewa ina son Maryam ba, duk zuwan da nake gidan nan ina kiranta mu gaisa ban taba cewa ina son ta ba, gata a nan tsaye idan na taba fada mata cewar ina son ta sai ta fada, kuma na gode Allah da ban taba furtawa ba, domin yanzu na gane irin tarbiyarku ba kuma za a je a tarbiyantar min da yaya haka ba, a gurinki yake abun kunya son yar aiki, a gurina abun alfahari ne ko ba komai zan zama mutum na farko da zan fara jiyar da ita dadin rayuwa, kuma zan auri mace mai tarbiya ba irinku ba” Kamal na aje numfashi Muhseen dake sauko daga upstairs ya dauka yana yatsina masa fuska. “Kai ne marar tarbiya marar hankali wawa wanda be san darajar na gaba da shi ba, ban da rainin wayo da rashin kunya ka isa ka shigo har cikin gidan nan ka ce zaka fadawa Mama maganar banza, waye kai a duk fadin Abuja? Kai kana da tarbiyar ne zaka nemi fada mata magana son ranka? Ko kuma saboda baka san darajar iyayenka ba shiyasa baka ganin kimar uwar kowa a duniya, kai ne baka da tarbiya kuma ba san inda ta fito ba, domin mu ba za mu iya ciwa uwar wani mutunci ba, amman kai zaka iya dan tsabar rainin wayo, ina ruwanka da yar aikin gidanmu? Ubanta ne kai? Ko yayanta? Sakare kawai mahaukaci daman sojoji ba ku iya komai ba sai hauka da fitsara” Kamal ya tabe baki. “Ka fadi duk abunda yai maka dadi a baki, ban yi mamaki ba ai kai ma dan wajen Fulani ne ko? No wonder” Yana fadar hakan ya duka ya dauki Ataa da take sume tare da ledar da zo da ita ya juya zai fita sai Muhseen ya nufo shi da sauri. “Karka kuskura ka ce zaka fita da ita, ko yankata Mama tai ba zaka fita da ita ba” “Mutuwa ce kawai zata dauke ni a yanzu na fasa kai Ataa asibiti amman ba kai ba balle wani naka” Ya fice da ita, Muhseen zai bi bayansa Momy tai saurin rike masa riga. “Karka je Muhseen kyale shi duk inda zai kaita ai dawowa za tai saboda nan aka kawo ta, kar kuje kuna abu kamar yara ka ka taushe fushinka dan Allah” Muhseen baya iya musawa Momy dan haka ya hakura ya zauna a kujerar jikinsa nata rawa kamar yadda zuciyarsa take yi. Mama Fulani kuma tana tsaye a gurin ta kasa cewa komai gaba daya mamaki ne ya kasheta domin a rayuwarta bata taba samun mutumen da ya iya tsawa gabanta ya ci mata mutunci kamar Kamal ba, cin mutunci ma a gaban yayanta, ita zai fadawa Maryam bata da tarbiya and be taba son ta ba. “Ni za a ciwa mutumcin a cikin gidana? Ni Kamal zai fadawa magana son ransa? Mi yake takama da shi dukiya ko aiki? To ya jira abunda zai same shi, ita kuma bar ta dawo” Mama Fulani na rufe baki Zee ta shigo dakin tare da Inteesar dauke da manyan kuloli, suna kallon yanayin mutanen falon sun san akwai abunda ya faru sai dai ba zasu iya gane ko minene ba. A gaban Momy suka dire kulolin sai Mama Fulani ta daka musu tsawa. “Ke Zainab ku dauke abincin ku maida wai ba na ce Ammy ta daina min shisshige akan bakina ba? An fada mata ban musu abinci ba ne ko?” Zee ta dago ta kalleta tana kokarin danna fushinta. “Na ga ai kamar ba bakinki ba ne bakin Abbah ne” Muhseen ya zaburo mata. “To rashin kunya za ki mata ko? Ban ballaki Wallahi” “Ba rashin kunya ba ne Ya Muhseen magana ce kawai” Ta bashi amsa tana kallonsa. “Dauki abincin ki fice da shi aka ce” Muhseen ya fada sai Momy ta dakatar da shi. “Aa ku aka kawo wa abinci? Ai ni aka kawowa ina ruwanki, Ke tashi ki tafi Zainab ki ce na gode” A tare suka mike tsaye Inteesar da Zainab suka fice...            Momy ta kalli Mama Fulani cikin yanayin damuwa ta ce. “Wallahi ni dai bana son halin nan na ki Fulani, miye a ciki dan ta dauko abinci ta kawo min Fisabilillahi?” “Shishhigi ne da ita kuma na fada mata bana son haka, ni da gidana wani zai min ba daidai ba?” “Amman ke ma ai ba gurinki na zo ba, ganin matar danki kawai na zo kuma gobe zamu koma, ni rigimar nan taku ban san ranar da zata kare ba, Siyama da Husna ku tashi ku yi sallah muje mu duba ta, Rukaiya da Maryam da Baby ma ku shirya muje” Sai a lokacin Husna da Siyama suka motsa domin tun da aka fara fadan suka make guri daya kamar basa nan, ba halinsu bane kuma ba halin Momy ba ne masifa ta kan yi amman sai idan rai ya bace sosai. Gaba dayansu suka tashi suka nufi upstairs Rukaiya na fadin abunda Kamal yai be kyauta ba, Husna na taba mata duk kuwa da bata san shi sosai ba, sai dai ta taba ganinsa sau biyu tare da Aliyu. Muhseen ma tashi yai ya fice daga falon cikin bacin ran abunda Kamal yai wanda be sake shi ba har yanzu. Momy ta kalli Mama Fulani. “Fulani Wallahi ku canja wannan zama na ku, tun yaushe ake abu daya? Kishi fa ba hauka ba ne, Fisabilillahi haka za ku taso kuna abu a gaban yayanku kuma manyan yaya ba ko kanana ba? Wannan ai bara kan yayanku kuke yi Wallahi” “Alhaji be auro Ramatu ba sai da amincewata kuma sai da ta yarda zata min biyayya, dan haka bata isa ta yi jayya da ni ba idan kuma har ta ce za tai nasan tsaf Alhaji zai sake ta komai yayanta” Momy dai ban da kallon Mama Fulani babu abunda take, ta sani Alhaji Hamza yana son Ammy sosai amman yadda Fulani take mata yana kyaleta abun har mamaki yake ba, duk kuwa da irin masifarsa domin shi mafadacin mutum ne sosai. Guraren la'asar Momy ta shirya ita da su Maryam, Rukaiya, Baby, Husna da kuma Siyaka suka fito harabar gidan sai Momy ta aika aka kira Inteesar da Batulu, Zee da Humaira suka shiga mota uku suka dauki hanyar asibitin. ALIYU POV. A lokacin da ya bar asibitin gidansa ya koma ya, yana shiga ya samu guri ya kwanta ba dan yana jin bachi ba sai dan ya samu sauki abunda ke zuciyarsa, matsalar iyeyen Rahma da kuma ciwonta a dayan bangaren kuma ga Ataa ta ta tsaya masa arai a yanzu yake tunanin ta ina zai fara taimakonta, what is best now is ya taimaki mahaifiyarta ta samu lafiya, sai dai be san ta inda zai samu mahaifiyar ba domin be san inda take ba, and Ataa bata bashi wata dama da zai iya sanin Familynta ba, sai dai yai ma kansa alkawarin zai taimake ta tai shiga rayuwarta ya nuna mata halinsa mai kyau da be taba nuna kowa ba, wata kila hakan zai sa ta aminta dashi har ta bashi damar sanin inda mahaifiyarta take, and ya ma kansa alkawarin ba zai sake bari a takura mata a cikin gidan nan ba, shine mataki na farko da zai dauka. Haka dai yai ta tunaninsa ta bangaren Rahma kuma idan ya fara sai ya rasa ta ina zai tuke, zancen neman wata kodar a yanzu be ma taso ba, ba dan kudi ba sai dan gudun kar a samu irin wacan matsalar idan kuma ba a samo mata wata ba, hakan na nufi nan da wani lokaci zata mutu kenan? Ko kuwa akwai wani magani da za a bata wanda zai saka kodar ta samu lafiya, ya kamata ya san wannan, idan ma zaa samu kodar a yanzu to dole ne sai ya ga mai ita kuma ya yi magana da mai ita ya aminta, da kuma amintaccen likita ba kamar Doc Asim ba. Idan kuma ba za a samu ba ya zame masa dole ya cire tashi daya ya bata domin yana son ganin matarsa a raye, and zai iya sadaukar mata da komai na sa ciki kuwa har da ransa idan da dama. Yana kwance Siyama ta kira ya ga kiran amman ya ki ya daga domin ba shi da time din wani magana ko wani abun dabam a yanzu, sam ya manta da zancen zuwan Momy ma tsabar tunanin daya saka a gaba. Bathroom ya shiga yai wanka ya fito ya shirya cikin wasu kayan ya fito yana ta kamshin turare ya sauko kasa ya nufi wata motar dabam ba wacce ya shigo da ita ba ya shiga ya dauki hanyar asibitin.   Ko da ya shiga dakin da Rahma take ya same ta zaune saman gadon mahaifiyarta kuma akan kujera suna ta kuka, ba a fada masa ba, ya san cewa mahaifiyar Rahma ta fada mata gaskiyar ciwonta. Ganinsa yasa mahaifiyar ta tashi tana share hawayenta ta fice daga dakin shi kuma ya karaso ya zauna a kujerar da ta tashi tana ta kallon yadda Rahma take kuka. Hannunsa ya kai ya kama hannunta yana fadin “An fada miki gaskiyar ciwonki kenan?” Sai ta kalleshi cikin hawaye ta ce. “Ina son rayuwa Aliyu, amman rayuwa bata so na, tun ina karama na ke ta fama da matsalar kodar nan, ima gidan aurena aka cire min daya saboda ta lalace, dayar ma aka ce sai an samo wata a dasa min, duka yaushe aka min kashen koda da har za a ce wannan ta lalace?” Tashi yai ya koma saman gadon kusa da ita ya zauna ya ja zuwa jikinsa ya rumgume cike da tausayinta....Gyara kanta tai a kirjinsa tana hawaye. “Babu abunda Allah ya rage ni da shi sai lafiya da haihuwa, ina da Uwa Uba yan'uwa miji duka a raye kuma duka suna so na, amman ba ni da lafiya kuma ban haihuwa, yanzu idan na mutu na zama mai yankaken baya kenan?” “Za ki samu lafiya Rahma sai mu cigaba da neman haihuwar ki daina zancen nemam haihuwar nan a yanzu” “Wata kila zan iya samun ciki na haihuwa ban mutu, amman zancen samun lafiya na warke kamar kowa na san ba zan taba samu ba, a da na yi zaton na warke idan aka dasa min wannan kodar amman sai gashi yanzu kuma ance ta kone” “Dan ta kone ba shi yake nufin ba zaki rayu ba, kika sani ko ki samu sauki mu cigaba da rayuwarmu” “Samun sauki ba abu ne mai sauki ba Aliyu, samun saukina yana nufin samun wata kodar, kai ma kuma na san ka fara gajiya da ni, Mommy ta fada ka ce ba za a sake samo wata kodar ba...” Dago kanta yai ya rika fuskarta. “Ban ce ba ba a sake samun wata ba, amman dai ba ta bangaren Asim ba, saboda gudun abunda ya faru ya sake faruwa” “Amman da ada ne kome zai faru ai zaka aminta ya faru ni na rayu, amman a yanzu ka canja wata kila ka fara gajiya da ni ne” “Taya zan gaji da ke Rahma miyasa bakinki zai rika furta irin wadannan kalaman? Ai nasan da ciwon ki kuma na aureki a haka neman kodar nan da akai har aka dasa miki ita ba wayayi ba ni ba? Idan na gaji da ke ai ba zan dauki duk wannan dawainiyar ba, amman maganar gaskiya ba zan sake yarda a cutar da wata saboda ke ba, zam iya komai dan ki rayu amman ba zan kashe wani ko na gulgunta rayuwar wani saboda ki rayu ba, ba kuma zan yarda a cire ko da kowa dan zalinci a dasa miki ke ki rayu ba, ko da kuwa hakan na nufin idan ba a saka miki ba ba zaki rayu ba, ba zan zalinci wani na raya ki ba Rahma duk kuwa da irin son da nake miki I'm telling you this form the bottom of my heart, sai dai zan yi dawainiya da ke har ki samu lafiya” “Ko kuma na mutu ba, saboda kai ka san zaka iya auren wata mata idan bana raye amman ni na tafi kenan. What if maybe kana daukar dawainiyata ne saboda kai baka haihuwa ni kuma ba ni da lafiya, sai mu taru a haka mu mutu? Ban san yadda zaka dauki abun nan ba Aliyu, amman lokacin da ba Mommy ta fada min cewar koda ta ta kone, mutuwa ce farkon abunda ya fara zuwa min a rai, da kuma haihuwa idan na mutum ban bar baya ba, na tafi kenan, amman idan na haihuwa zan iya barin abunda za a rika tunawa da ni idan ana kalleshi” Murmushi Aliyu yai irin murmushin nan da yafi kuka ciwo, yau wai Rahma ce take fada masa wadannan kalaman yasan tana son haihuwa kamar yadda shi ma yake sonta, tabbas mai irin matsalar ta zai son ganin zuri'arsa ko ba dan mutuwa, shi kansa yana son haihuwa amman gudun shiga damuwarta yasa shi kawarda tashi. Iyakar abunda zai iya yi a yanzu nuna mata kalamanta basu bata masa rai ba, domin idan har ya bari bacin ransa yai tasiri akansa zai iya fada mata magana marar dadi ko kuma yai fushi da ita wanda yake ganin hakan be dece ba a yayinda da take cikin rashin lafiya. Ba karamin kokari yai ba na kai bakinsa yai kissing goshinta kamar yadda ya saba yana sauke ajiyar zuciya a hankali. “Ki kwantar da hankalinki idan kin samu lafiya za mu nemi haihuwa” “Wata kila matsalar da daga ni ne, da yanzu Mama Fulani da Momy sun saka ka kara aure saboda ka haihu, domin ko wannensu yai min gorin haihuwa, amman da yake ka boye musu gaskiya kace dukanmu ba mu da matsala sai suka daga min kafa suna ganin kamar wata rana zan iya haihuwa, ni ma haka na ke ta saka rai ni da iyayena shiyasa na dage gurin neman magani ashe matsalar ba daga ni ba ne” Sakinta Aliyu yai ya mike tsaye ya saka hannayensa aljihu ya tsaya gaban windows dakin yana kallon waje zuciyarsa na masa mugun kuna. Rahma kuma ta bishi da kallo tana hawaye, har ga Allah tana son Aliyu kuma tana kaunarsa amman matukar ta tabba matsalar daga shi ne dole zata hakura da shi ta auri wani saboda ta samu haihuwa domin ba zata yarda ta bar duniya ba tare da ta bar baya ba, and tana da tabbacin wata kila da ita ce da matsalar da ba zai zauna da ita ita kadai ba, da yanzu ya yi aure ko ma ya rabu da ita gaba daya kamar yadda mahaifiyarta ta fada mata a lokacin data labarta mata gaskiyar cewar matsalar daga Aliyu ne a wacan lokacin kamin rashin lafiyar ta kamata. Sai dai me wata kila idan babu Aliyu a rayuwarta ba zata iya rayuwa ba, wata kila ba zata iya komai idan babu shi ba, domin ta shaku da shi kuma tana kaunarsa irin kaunar da ba zata iya misaltawa ba. Aliyu be juyo ba har sai da yaji an taba kofar dakin an turo an shigo. Momy ce ita da siblings dinsa. Yayi kokarin boye damuwarsa amman ya kasa har sai da Momy ta karanci yana cikin damuwar a fuskarsa. Ita kuma tai saurin share hawayenta tana kokari kirkiro murmushi, tsaye sisters dinsa sukai suna mata sannu Momy kuma ta zauna a kujera tana ta duban yanayinta da na Rahma. Aliyu ya yi farincikin ganin Momy domin be tsammaci za tai saurin zuwa a yau ta duba Rahma ba saboda yawan complain din da take cewar Rahma bata son zuwa inda take, sai dai be yi mamaki ba dan yasan halin Momy da dattako da kuma maida komai ba komai ba. “Yanzu kuka zo?” Aliyu ya fada yana kai hannu ya riko hannun Inteesar, sai ta dawo kusa da shi ta tsaya tana dariya. “Tun dazun muka zo, ai na saka Siyama ta kiraka baka daga ba” “Na ga kiranta amman ban dauka tare ma muka zo ba, na dauka rokonta ne ya tashi” Sai dai duk sukai dariya ban da shi da yai maganar, sam ba zaka kalleshi ma ka ce shi yai maganar ba, daman haka yake ko abun dariya ya fadi na kasafai yake dariyar ba.Bayan sun gama ganinta Momy ta kallesu ta ce. “To ai sai ku wuce ku koma, kar likitocin su zo suce mun yi yawa, kuma mun baro Fulani ita kadai gashi beta gama fucewa ba” Aliyu ya kalleta kamar ya tambayi abunda akai mata har Momy take fadar hakan sai kuma wata zuciyar ta hana shi. Rukaiya ce tai kwafa “Wallahi kwata kwata Kamal ba shi da mutunci kuma ba shi da tarbiya” A take zuciyar Aliyu ta kwadaitu da son jin abunda ya faru amman ya kasa tambaya har sai da Zee da ke son ta ji labarin ta tambayi Rukaiya. “Mi Kamal yai hala?” Rukaiya da Maryam ne suka labarta abunda ya faru a nan Aliyu ya ji komai, wayarsa ya ciro kamar be damu ba ya nufi kofa rike da hannun Inteesar ya fice. Sai da ya fito daga ward din sannan ya turo Inteesar ta kira masa Zee, ita da Inteesar har a rigengen zuwa suke domin sun san Aliyu baya son jira, kuma abu kadan ya saka ransa ya bace. “Zainab So na ke ki kira min Kamal ki tambaye shi wace asibiti ya kai Ataa” “Ya Aliyu bana da number Kamal” Ya mika mata wayarsa ba tare da ya ce mata komai ba, tana karba sai taga number Kamal a sama sakawa tai a wayarta ta kira bugu biyu ya daga. “Hello Kamal ina wuni” “Lafiya kalau wake magana” “Zainab ce, wai Ammy tace a tambaya wace asibitin ka kai Ataa” “Ammy? Ko Mama Fulani dai” “Ammy dai” “Perry Hospital female ward room 104” “Thank you” Tana fadar hakan ta sauke wayar ta yi karya da Ammy ne domin ta lura da Aliyu baya son asan shi ya saka ta kira, da acce yana so da shi da kansa zai kirashi tun da abokinsa ba sai ya saka ta ba. “Ya ce Perry Hospital female ward room 104” Ta fada tana mika masa wayarsa, karba yai ya saki hannun Inteesar ya fice daga gurin. Ita da Inteesar suka dawo dakin da Rahma take. “Ku wuce kawai gida, ni zan tsaya a nan sai an jima Dan wajen Fulani zai maida ni gida” Sai da suka mata Allah ya sauwake sannan suka fita. Bayan sun fice ne Momy ta kalli Rahma da ke cikin damuwa ta ce. “Ciwo fa ba mutuwa ba ne, dan ba ki da lafiya ba shi yake nufi zaki mutu ba, ko babu kodar a jikinki idan Allah ya so sai ki ga ya raya ki” “Ba neman lafiyar ne abunda ya dame ni yanzu ba Momy, haihuwa ce abunda ta dame ni a yanzu, ina son na haihu kamin na mutu” “Duka dai na Allah ne, kuma idan yace yanzu abu ya kasance za ki ga ya kasance” “Wata kila da matsalar daga ni ne da zan iya samun sauki ko kuma wata mafitar, amman matsalar daga Aliyu ne na san ba zan taba samun waraka ba” Momy ta kalleta irin kallon nan na ban fahimci zancen ki ba. “Matsalar daga Aliyu ne? Kamar ya?” Rahma ta yi shiru bata ce komai ba, domin ta fahimci be fadawa Momy ba. A take hankalin Momy ya tashi fiye da da, domin a da tana daukar daga shi har Rahma ba su da matsala kamar yadda yake fada mata likitoci sunce yanzu kuma Rahma ta ce matsalar daga shi ne, amman miyasa be taba fada mata ba? Daman Rahma ta san da wannan ta rufa masa asiri take zaune da shi a haka ko kuwa daga baya ne abun ya bullo? Anya Mama Fulani ta sani ma kuwa? Har Momy ta bude baki zata sake tambayar Rahma sai ga wani Doc ya shigo tare da nurses kusan biyar suka hau duba Rahma suka bata magani sannan suka bawa Momy takardar sallamarta domin su a gurinsu ta ji sauki tun da ta farfado kuka bata jin ciwon komai sannan kuma an riga an san matsalar koda ne, sun kuma dorata akan magani. Daman haka suke yi sai dai idan mutum yana son ya cigaba da karbar magani a asibitin sai ya bukaci su barshi yai ta biyan kudi yana karbar magani har ya kare. Momy ta yi kokarin nuna farincikinta duk da irin tashin hankalin daya same ta na jin gaskiyar maganar cewa matsalar haihuwar daga Aliyu ne, har ga Allah ta jidadin samun lafiyarta domin ko bata san inda Rahma ta fito ba za tai farincikin samun lafiyarta a matsayinta na musulma balle kuma matar danta ce dan ta take aure. After like thirty minutes da fitar likitan Mommyn Rahma ta shigo da kanenta ai ko suka hau murna kamar su cinye Rahma sun jidadin ganin an sallame a take hakan na nuna jikin nata da sauki keman kuwa da kasancewar kodar na ta a kone yake. “Mahaifinki ya ce ya saka cigiya a gurin likitocin daya sani a nemo duk inda koda take kuma ko nawa take za a siya miki, kin kwantar da hankali lafiya zata samu In-Sha-Allah” Mommyn Rahma ta fada tana dariya sai dai ita Rahma bata wani farinciki sosai, domin tana cikin damuwa a yanzu. Momy ce ta kira Aliyu ta fada masa an sallami Rahma kuma ya zo ya maida ita gida, da murna ya amsa mata sannan tai hanging call din ita da farinciki tana kallon Rahma, sannan gaisuwa ta biyo bayan tsakaninta da Mommyn Rahma har suka dora da labari.ATAA POV. Ban san adadin wannin dana dauka a sume ba, shin sumar ma nai ko kuwa dai wata duniyar na tafi na dawo domin Nana nai ta gani da kuma wata rayuwa da muka kai da ita a can baya, da kuma ganin da cikin wani daki mai kamar na kasa ba kuma kasar ba, shin haka suman yake ko kuwa fitar hankali ne kawai daga jikin duk ba zan iya tantancewa ba. Da wani irin karfi marar misaltuwa na ji na dawo duniyar motane da dabbobi har ma da sauran hallitu, duniyar da ke cike da kazanta da gurbatacciyar rayuwa da ba kowa ke tsira cikinta, wasu abu nake gani su ba mutane ba kuma su ba aljannuna ba, ganina nai kasa bana iya tantance ko mienene sai dai ina ganin kan abun yana yawa kuma suna sanye da fararen kaya. Daga bakina har hanci da ido numfashi suke fiddawa da karfi wani kuma na shiga da karfi, wani abu ne a kirjina kamar dutsin guga da zarar numfashin nawa yai kasa sai su goga shi da dan'uwansa su manna min shi a jiki sai na ji makamancin abunda na ji dazun, haka sukai ta min har numfashin nawa ya daidaita, sai sannan na soma ganin likitoci su uku ashe mutane ne ba aljannuna ba kayan likitocin na su ne nake gani farinsu kamin idon nawa ya waye. “La'ilaha illallahu Muhammadu Rasulullah Sallalahu Alaihi Wassalam” Shine abunda ya fito daga bakina sai na lumshe ido ina fitar da numfashi a hankali. Dayan daga cikin su ne naji yai hamdala ga Ubangiji da alama shi din musulmi ne. Sai na ji dayan ya kira sunana da hausar da da bata fito sosai. “Aasha” “Na'am” Na amsa ina kallonsa sai dai muryar tasa har yanzu kasa kasa nake jinta. Dauke ni sukai daga saman wannan gadon suka dora ni akan wani suka turani zuwa wani dakin na musamman a akan gadon dakin suka dorani sannan sannan suka saka min drip dayan kuma ya saka min bandeji a bayan kaina, sannan suka juya suka fita. Lumshe ido nai ina kokarin tuna abunda ya faru sai na ji an turo kofar an shigo hakan yasa na bude idona sai na ga Kamal cikin shiga ta manyan kaya ya doso inda nake cikin yanayin damuwa. “Ataa” Na kalleshi ina kokarin amsawa sai ya kai hannunsa ya taba jiki. “Kina jin wani abu yanzu?” “Bana jin komai” Murmushi yai ya gyara min kaina da gashina. “Sannu” Na gyada masa kai. “Likito ci sun ce abarki ki yi bachi, zan je gida na dawo ke kuma ki samu bachi kinji” Nan ma kan na gyada sannan na ce “Na gode” “Ba komai Allah baki lafiya” “Amin” Na amsa cike da nauyin baki sannan ya juya ya fita, ni kuma na lumshe idona bachi wahala yai gaba da ni. Wata kila na kai wa biyu ina bachi kamin na farka, idona na fara budewa ina ta kallon farin silin dakin warin asibiti na soma ji kamin na kamshin turaren Aliyu ya biyo baya, dagowa nai kadan sai na ganshi zaune saman kujera yana ta kallona da cat eyes dinsa ko kyaftawa ba yayi. Nima idon ma sakar masa ina ta kallon fuskarta, sai a yau ake kara tantance kyauwunsa hanci ya sauko sosai ga manyan ido masu daukar hankali. “Ba na ce ki daina kallona ba?” Yayi maganar kamar shi ba kallona yake ba, yana takura idan ana kallonsa sai dai shi ya iya kallon wasu har sai ka soma tsarguwa. Rumtse ido nai ina turo baki, sai na ji an buge min bakin da sauri na bude idon na kalleshi yanayim yadda yake sai yai min kamar ba shi ya bugar min bakin ba sai dai hakan be hana na zaburo masa. “Mi na maka zaka dake ni?” Kallona kawai yai be ce komai ba ya mike tsaye yana saka hannunsa na dama aljihu sai kuma ya kai dayan hannun sai taba kaina. “Me zaka mata? Bayan marin da Mama Fulani tai mata wani zaka mata kuma?” Kamal ne ya shigo hannunsa rike da leda yana fadin yana tare da doso inda nake kwance, Maganarsa bata hana Aliyu tana kan nawa ba, kamar ma be san da shigowar Kamal a dakin ba haka yai domin ko inda yake be kalla ba ni kawai yake kallo yana taba jikina da alama so yake yaji idan jikin nawa da zafi ko sanyi. “Ashe dai ba Kamal kadai yake iya kula yar aiki ba, idai ko haka ne ya kama ka sauke girman kan nan naka Aliyu” Dagowa Aliyu yai ya kalli Kamal. “Ba a fada min abunda zan yi sai dai ni na fadawa wasu abunda za su yi, a kasa da ni kake Kamal kasan ma kasan takarmin kafata, ya zama dole ka min biyayya kuma ka kalleni da daraja ba zan sake musayar yawu da irinka ba” “Daman ai ba ku saba ganin kowa da daraja ba, sai mai arziki ko wanda arzikin ya nemo saninsa, ban yi mamaki ba kai ma ai dan wajen Fulani ne” “Yes dan ta ne, mai sanin darajarta ,kar bakinka ya sake ambatar sunanta idan ba haka ba sai ka yi nadamar saninta a rayuwarka, and i warned you karka sake shiga rayuwar yarinyar nan? Ashe kare ne kai marar zuciya, yanzu kuma umarni na ke baka ka dauke ta ka maida ta gida kamar yadda ka dauko ta kamin nan da one hour” Aliyu ya fada yana hada babban yatsansa da na uku sai suka bada wata kara kamar an yi tafi, sannan ya nufi kofa ya fice ransa a bace. Da wani kallon wulakanci Kamal ya bishi yana tsaki kamin ya juyo kaina ya kalli ya sakar min murmushi. *.ZAKI By Khadeeja Candy 27... Kallo yake da mamaki yana kara gyara zamansa. “Waya yaudare ki Ataa wane hali ne ya jefa ki ke da mahaifiyarki?” Hade kukana nai sannan na sauka daga kan gadon nai tsaye ina kallonsa. “Na ji sauki za mu iya zuwa gida?” “Gida gurin Mama Fulani ko gida gidanmu?” “Ka dauke ni daga asibitin nan ya kai ni wani guri inda ba zan ji kamshi magani ba” Ido ya sakar min yana ta kallon fuskarsa na bayyana irin tarin tambayoyin da ke zuciyarsa. Sai kuma ya mike tsaye ya aje kazar a kan wani karamin dorowa ya fice daga dakin, ya bar ni ina ta zullumi da tunani wata kila idan an koma Mama Fulani korata za tai da gaske ko kuma ta sake min wani dukan, ni da sam ban jidadin da Kamal ya kawo ni asibitin nan ba domin na san ba da amincewar ta ya kawo ni ba, kuma yadda Aliyu ya fusata ita zata iya fusata ko dan shi. Tare da wata likita mace ya dawo ita tai min umarni da na zauna na zauna kamar yadda ta ce ta duba ni sannan tai rubuta a wata takarar guda biyu ta mika masa ta fice. “To muje” Ya fada yana kallona sai na wuce gaba ina ta jin kunya domin kaina babu dankwali gyale ma balle Hijab, ya dauko ledar kazar ya biyo bayana, ni dai tafiya kawai nake ba dan inda zan biba domin ban san kan asibitin ba ina ta bin inda nake sa rai da zaton hanya ce har na fito daga ward din ina jin kunya sai dai na lura kowa be kula da ni ba. “Nan za mu bi” Ya fada yana daukar wata hanyar dabam ba tare daya jira ni ba. Haka na bi bayansa har muka isa wani gurin da ake aje motoci ya nufi motarsa ya bude ya shiga ni kuma na bude front seat na shiga na zauna, be kalli inda na ke ba har muka isa gidan, a tsakanin asibiti da unguwar tafiya ce mai nisa ban san ko'ina ba a garin Abuja balle na ce ga unguwar da muka fito ko muka wuce amman duk da tsaye tafiyar Kamal be ce min komai ba kuma be kalle ni ba har ya faka motarsa a harabar gidansu. Ban tana shiga gidan ba sai yau, shi ma gida ne babban mai bangarori da dama domin shi ya fi part hudu duk ban tsaya na tantance ba sai dai shi gidan kasa ne ba kamar na su Mama Fulani da yake gidan sama ba. Shi ya fara fitowa ya rufe motar sannan na sauko daga motar na rufe na fi bayansa cikin rashin sakewa da bakunta a wani gidan da ban ta6a shiga ba. Yana gaba ina baya har muka isa cikin gidan, da kunya sosai na shiga cikin gidan, su kan na su gidan tsakar gidane farko kamin ka kai ga kofar shiga falon, wasu yan mata biyu na gaban murhu suna suya naman rago sai kuma wata dattijiwa mai kamar yar aiki tana yanka nama ita da wata mata da na ji Kamal din ya kira da Mama. “Mama ga bakuwa na kawo muku” Matar ta kalleni tana murmushi sannan ta kalleshi ta ce. “Maraba da ita ina ka samo mana wannan bakuwar?” “A fara bata guri da abinci ta ci ta koshi zata ba ku labari da kanta” “Ina wuninku” Na gaisheta cikin ladabi sai ta amsa min tana ta kallona sai kuma ta kalli Kamal tai murmushi. “Sai Soja” Daya daga cikin yan matan ta fada tana dariya sannan ta doso inda nake ta rika hannuna nufi cikin falon gidan. Ba laifi an gyara ko'ina an kuma turare falon da turaren Awwaba ko ina sai kamshi yake irin na yan sudan. Da kanta ta zaunar da ni saman cushion tana ta kallon gashin kaina daya bazu a jikina.“Karki ji tsoro babu abunda zai iya yi” Kamal ya fada min yana murmushi ganin kamar hankalina ya tashi da jin kalaman Aliyu. “Ya ce ka maida ni gida” Kallona yai sai kuma ya kai hannu ya bude ledar hannunsa kaza ce mai zafi da yoghurt ta sha mai har takardar da aka saka ta ciki ta narke da mai. “Ban san me zan siyo miki ba shiyasa na siyo miki kaza yar marmari, wata kila kuma ba ki ci abu mai nauyi domin na ga jikin na ki kamar na baby doll” Ya fada fuskarsa da murmushi yana daukar cinyar kazar ya miko min, sai na kasa karba, na kuma kasa sakewa ba duk irin son nama da nake sai na ji ya fita rai, gaba daya hankalina yana can gurin Mama Fulani da Aliyu, tsorona daya kar korar da Mama Fulani ta ce zata min ta tabbata ga shi Aliyun ma ya fusata wata kila shi ma korata zai yi. Idan ko har suka kore ya zama anyi ba ayi ba kenan, abunda na zo nema be samu ba. “Karbi ki ci, na fada miki karki ji tsoro, babu abunda zai same ki” Hawaye ne suka sauko min na kasa ce masa komai kuma na kasa karbar naman. “Kin fi son ki koma gidan nan?” Na gyada masa kai sai yai murmushi “Zan maida ke amman ba yanzu ba, Aliyu be isa ya bani umarni na bi ba, wani fadin rai nashi da hargaginsa na banza ba zai saka nai abunda zai dauka cewar tsoronsa na ke ba, ban san abunda kika yi daya saka Mama Fulani ta mareki ba, sai dai ina ganin kamar be dace tai miki hakan ba dan kawai kina aiki karkashinta” Kasa nai da kaina na saka hannu na share hawayena, murya can kasa kasa na fara magana. “Zan jure komai za a min a ko'ina matukar hakan na nufin silar farincikina, samun lafiyar mahaifiyata shine farinciki a yanzu shine abunda na ke bukata kuma shine dalilin zuwana aiki a nan, ka kyale na wulakanta ta dake ni idan tana ra'ayi ta yi min abunda duk ta ga dama, zan jure har na cimma cikar burina” “Zan taimake ki Ataa zan taimake ki mahaifiyarki ta samu lafiya” Kallonta nai idonta na zubar da ruwan hawaye na ce. “Bana bukatar taimakon kowa a yanzu, bana son kowa ya taimake ni na fi yarda da nai komai da kaina, da sunan taimako wani ya yaudare yaudarar da ta jefa mahaifiyata da ni a cikin wannan halin, ba zan sake yarda da taimakon kowa ba, matukar ba talaka ne dan'uwan ba”“Sannu bakuwa ya sunanki hala?” “Aisha” “Kai kai sunan Mamanmu ne” Ta nufi wata hanya da ke kamar corridor sai ta ga ta fito da gorar ruwa da kofi a hannu ta kawo gabana ta aje min. “Ki fara shan ruwa kamin abinci ya zo” “Na gode” Na fada ba tare da na kalli ruwan ba, sai ta tashi ta fice daga falon ta bar ni nan zaune ina ta kallon yadda aka kawata ko'ina na falon. Wata budurwar ce ta shigo dauke da farantin nama da yaji a gafe ta aje mika min. “Ga shi ki saka a baki bakuwar yaya” Ta fada da kamar zolaya. “Ina Kamal din yake?” “Ya fita yanzu amman ya ce mu kula masa da ke” A yanzu ma murmushi take tana maganar ni kuma na mike tsaye ina kallon kofa na ce. “Bari na leka gidan Mama Fulani kamin ya dawo” “Okay kin santa ne?” “Eh na santa” Shine kawai abunda na fada mata na nufi kofar ina ta sauri na fito daga falon. “Aa har kin fito?” “Eh nan zan je gidan Mama Fulani na dawo” Na bawa matar dazun amsa sai ta amsa da. “Okay sai kin dawo” Kamin na isa gate din gabana nata faduwa ina ganin kamar haduwa zan yi da Kamal ya dawo ya hana ni fitar, ina samun nasarar ficewa daga gate din na tsallaka titi da sauri na buga gate din gidan Mama Fulani mai gadin ya bude min na shiga da sauri kamar wacce tai sata. Gadan gadan na doshi cikin gidan duk irin faduwar gaban da nake ji da tsoro arba da Mama Fulani sai na danne shi na tura kofar falon na shiga da sallama. Tana tsaye tana magana da suka yan matan nan na dazun da suka zo baki da kuma yayanta ta juyo ta kalleni. “Me kika dawo ki yi?” Durkusawa nai daga inda nake tsaye bakin kofar na hade hannayena ina rikonta. “Dan Allah dan girman Allah ki yi wallahi ban san ya kai ni asibiti ba, kuma ban ce ya kai ni ba, dan Allah karki kore ni” “Da ya kai ki asibiti da kar ya kai ni uwarsu daya ubansu daya a gurina, amman tabbas yau ba za ki kwana a gidan nan ba” “Ki tausaya min dan Allah saboda Mama nake wannan aikin, bata da lafiya kudin maganinta nake nema” “Ni nan da kika ganni ba ni da uwa da uba duka sun mutu marainiya ce ni, kara ke ma har da iyayenki a raye, wuce kije ki hada kayanki yanzu nan bana son ko minti talatin ki kara a gidan nan” Ta fada cikin daga murya tana nuna min kofar fita. Siyama ta kalleta ta da tausayawa ta ce “Mama ki yi mata hakuri idan ta sake sai ki koreta” Sai Rukaiya tai karaf ta ce. “Wallahi ni bana ma son minti biyar ta kara a gidan nan wacan yarinyar da kike gani tun da ta zo kullum sai wani mummunan abu ya faru” “Za ki wuce ko ba zaki wuce ba” Mama Fulani ta daka min tsawar da ta sakani mikewa tsaye a razane na fice da sauri. Garejin na dawo na zauna ina ta kuka mai karfi wai ko wani zai ji ya zo ya tambaya dalilin kukana yajd ya bata hakuri amman babu wanda ya zo har na ji muryarta tana kiran Zaharadden direba. “Ki fito yanzu nan ko na shigo cikin na ci miki mutumci” Da sauri na tashi na dauki jakar tawa na nufi garden na dauko ragowar tufafin dana shanya tun rana na saka a ciki na dawo garejin na saka sauran da musasshiyar farfesun kazar dana shanya na saka cikin jakar da siyayar da Kamal yai min, sannan na saka Hijab dina na fito ina hawaye na tsaya jikin garejin ina kallon kudin da take ba wa direban. “Ka tabbatar ta shiga mota sannan na mika mata sauran kudi, idan an isa kaduna ta hau motar sokoto ai tasan gidan ubanta idan aka sauke ta a can” “To Hajiya” Ya fada yana karbar kudin tare da zagaya wa wajen motar ya bude ya shiga. “Zo ki wuce mun rabu da kaya” “Kudin aikina fa?” “Aikin da ko wata ba ki yi ba? Je ki turo ubanki ya zo ya dibar miki” “Ubana baya duniya Hajiya, ya tafi idan zan ki je zan je kowa zai je, amman Allah zai dibar min hakkina” Shine kawai abunda na iya fada cikin kuka na nufi motar na bude na shiga, ina jinta tana ta zagina. Hawaye ne suke ta min zuba har muka isa tashar, a lokacin da direban yai farkin na bude zan fita sai na ji ya ce. “Ki yi hakuri da rayuwa, haka take zuwa juyi juyi Allah ya sauwake mana talauci ni da ke mu daina zama karkashin kowa” Da na kalleshi sai na ga hawaye a idonsa. “Amin” Na amsa sannan na sauka daga motar shi ma ya fito, sai da yaje gurin yan Union ya hannata musu ni ya basu kudin motar zuwa kaduna da kuma kudin motar Kaduna to sokoto sannan ya ciro dubu biyu ya mika min. “Gashi ki rike wannan Allah ya kai ki lafiya sai wata rana” “Na gode” Na karba da hannu biyu ina ta hawaye kamar wacce akai wa ido dan hawayen kawai. “Lafiya Mutuwa akai miki?” Daya daga cikin mutanen ya tambaya. Sai na girgiza masa kai ina jan magina. “Aa ba mutuwa akai min ba” “To Allah ya sauwake” “Amin” Shi ya nuna min motar da zan shiga sannan ya bawa direban kudina da kuma kudin motar da zai saka ni ta Kaduna sannan na shiga na zauna muna jiran karin wasu mutum biyu. Ban dade da zaman ba aka kira sallah la'asar sai da aka kira sallar na tuna da cewar ban yi sallah azahar ba, sauri na fita daga motar na nufi gefen masallacin nai alwala da butar su sannan na nufi wani dan daki dana hango mata na shiga na shiga ciki nai sallah, na fadawa Allah bukakata kuma na kai masa kukana na kuma roki mafita akan dukan lamura na. Ba bar tashar ba sai biyar da kwata sannan direbamu ya kama hanya.ALIYU POV. Da mugun bachin rai ya fita daga asibitin yana cikin motarsa Momy ta kira shi ta fada masa cewar an sallami Rahma kuma ya zo ya tafi da ita, jin wannan labarin yasa ki sakewa daga bachin ran da yake ciki sai ya dauki hanyar asibitin. Ko da y shiga ciki ya samu Momy da Mommy Rahma suna fita Rahma na zauna tare da kanenta guri daya fuskarta babu walwala, ganin Aliyu ya saka kanen nata suka tashi daga saman gadon suka dauki wasu kayan da za a tafi da su suka fice. Da murmushi Aliyu yake kallonta amman ita ka kasa sakewa kamar ba ita aka sallama ba. “Amman na ce idan mun wuta yau zuwa gobe za mu tafi da ita can sokoto ta samu kula kuma idan tana kusa da mu ita kanta zata fi walwala” Mommy Rahma ta fada har Aliyu ya bude ba ki zai yi magana sai Momy ta shiga kuma ta shanye duk wani abu da yake da niyar fada. “Eh nima na yi wannan tunanin hakan zai fi, shi kanshi Dan wajen Fulani ai ba zai ki ba, Allah dai ya bata lafiya muma ai goben za mu koma” Shiru yai be ce komai ba, saboda Momy ta saye bakinsa. Mommyn Rahma da Momy tare suka jera a gaba suna tafiya shi kuma ya jero shi da Rahma suka nufo gurin da ake aje motoci. Wata motar Mommyn Rahma da kanenta suka shiga Mommy kuma ta shiga gidan baya Aliyu da Rahma suka shiga gaba. Sai da ya fara shiga har cikin gidan Mama Fulani ya sauke Momy har sisters dinsa suka fito suka ga Rahma ban da Mama Fulani da take jin sai dai Rahma ta fita daga motar taje ta gaisheta. Bayan Momy ta fita ya wuce da Rahma gidansa, bata ce masa komai ba shi ma be ce mata ba har suka isa tana kao hannu ta bude motar sai ya rike dayan hannun wanda hakan yasa ta kalleshi. “Rahma kamar ba ki murna da sallamar nan da aka miki?” “Miye abun murna a gurin gawar da aka kai asibiti? Ai kasan daga asibitin sai kabari, ba warkewa nai gaba daya ba, to me zai saka ni murna?” “Wani ya baki tabbacin cewa ba za ki warke ba? Ko kuwa kina da shaidar cewar mutuwa za ki yi saboda kina da wannan ciwon” “Za ka iya bani tabbacin cewar zan warke na tashi kamar kai? Ko kuwa zaka ba ni tabbacin cewar wannan ciwon ba zai yi ajalina ba?” Ta aika masa da tambaya cikin tambaya ba tare da ta bashi amsar tambayar da yai mata ba. Fita tai daga motar ya zagaya gefenta ya bude mata motar ya fito da ita ta rumgumeta sai ta karasa fashewa da kukan da take ta kankame shi sosai tana shakar turaren jikinsa. “Bana son na rayu da wani namijin baya kai Aliyu, ina son ka sosai, ko da bana aurenka ba zan iya jurar ka kula da wata macen kamar yadda kake kula da ni ba, ba zan bari son wata mace ya shiga zuciyarka ba dan Allah ka min alkawari ko bayan raina ba zaka auri wata ba” “Mi zai saka na auri wata bayan kina raye? Ko wace ta cancanci wani gurbi a zuciyata bayan ke Rahma? Be kamata kina irin wadannan tunanin ba” Akwai abubuwa da yawa da ba su kamata na aikata su ba Aliyu amman dole na aikata, a zuci tai wannan maganar tana nasalta yadda zata rayu ba tare da Aliyu ba na dan lokaci kamin da dawo masa kuma ta dawo da farincikinta da cikar burinta na haihuwa. Rikata Aliyu yai suka shiga cikin falon zuciyarsa cike da tausayinta duk kuwa da irin maganganun da tai masa dazun suna cikin ransa. ZAKI By Khadeeja Candy 28... ATAA POV. Misalin goma na dare muka isa Kaduna, a cikin tashar direban ya sama min guri na kwana bayan na yi sallah, washe gari ma sai da na siya pure water sannan nai sallah asuba, bayan ruwan naira goma ban sake saka komai a bakina domin jin nai bana bukatar komai kuma bana jin yunwa, da asuba muka kamo hanyar sokoto daga Kaduna, ina ta jin kamar zan yi amai a motar saboda kaurin mai da tafiya mai nisa wacce ban saba da ita ba. Ana gama sallah azahar muka shigo sokoto, ba dowowar dadi nai ba amman tuna cewar da mahaifiyata zan gana sai na ji sanyi, a wani bangaren kuma ina ta zullumi da tunanin abunda zan fada mata domin na san ba zata ji dadi idan na fada mata an korono ba, gashi kuma ban samu kudi ba. A babbar tasha muka sauka na dauko jakata da dubu daya da dari biyar da sauran canjin da na siya ruwa da su cikin kudin da direban Mama Fulani ya ba ni. Sai da na kawo bakin titi sannan na tari napep na shiga na fada masa inda zai kawo ni. Daga tashar zuwa Clapperto road dari da hansi ya kawo ni na bashi kudinsa na fita zuciyarta cike da zullumi da tunanin karyar da zanyi, har ina tunanin fara zuwa gidan Maman Salma sai kuma na wuce gidansu Farida kai tsaye. Wani dan karamin dakin kwano ne akai a gafen gidan wanda akai masa fuska daga can gabans ta yadda wanda yake cikin dakin baya ganin wanda zai zo wanda kuma zai zo baya iya ganin na ciki. Ina ta mamakin miye a gurin domin ban san da dakim kwanon ba kamin na tafi,. Da sallama na shiga cikin gidan sai Farida ta fito waje da sauri tana washe hakora. “Oyoyo Ataa” Rumgume ni tai duk da ina cikin bacin rai hakan be hana ni murna ba na rumgumeta muna murna da ganin juna. “Ina jin muryar na ce ke ce” “Ni ce fatar na same ku lafiya” “Lafiya kalau” Na sake ta na nufi dan kitchen din da nasan na bar Nana a cikin kamin na karasa ta ce. “Ai am maida Nana dakin waje” Cikin yanayin rashin jindadi ta fada fuskarta na nuna haka. Ban tambayi dalili ba sai dai naji faduwar gaba jin hakan, sai na juyo na fito daga gidan gaba daya na nufi inda kofar dakin kwanon take Farida na biye da ni a baya yanayinta kamar mai jin tsoro. Mutuwar tsaye a bakin kofar dakin kwanon na saki jakar da ke hannuna ina kallon Nana da ke kwance kamar kare domin babu tsoka a jikinta sai ƙassa, kanta ba dankwali gashin kanta ya tsire an rufa mata wani zane dakin gana daya wari yake warin kashi da fitsari, kallo take ba dan ta ganeni ba sai dan mutum take gani ban san lokacin da hawaye suka fara min zuba ba zuciyata ta rufe tai min wani irin mugun nauyi.. Daker na iya daga kafata na shiga cikin dakin hawaye na sauko min wasu na bin wasu. Kusa da ita na je na zauna ina kiran sunanta. “Nana Nana Nana” Shiru bata amsa min ba, sai kallona take kamar bata gane ba. Hijab dina na cire na na aje Farida na tsaye tana kallona har na janyota domin bana iya daukarta gaba daya bakin kofar dakin na kawo ta na aje, na fito da komai na dakin na nemi tsohuwar tsintsiyar mu da naga a cikin kaya na share dakin, na dauki roba na shiga ciki na debo ruwa kasancewar cikin gidansu Farida a akwai rijiya, na dawo dakin na zuba ruwan na wanke na masa tas, duk abunda na ke Farida na tsaye tana kallona ta kasa komai, Hijab din nawa na saka na je gawon nama na siyo omo da kudin hannu na siyo fura da nono da madara na dawo, ko da na dawo Farida ta shige cikin gida, ni kuma na sake sakawa dakin omo na wanke shi ya cire duk wani karni da warin da yake sannan na dauko turaren da Kamal ya siya min na saka duk da kasancewar na jiki ba hakan be hana dakin kamshi ba, zane da zane na hada na zagaye sannan na sake debo wasu ruwan na kai na jata a haka na kaita gurin na zuba mata ruwa nai mata wanka ko ina na jikinta sai da na wanke sannan na sake dawowa da ita a cikin tufafi na dauki wata riga da Aliyu ya bani na saka lokacin da nai rashin lafiya ta manya na saka mata na daura mata dankwalin sai na aje ta a waje saboda dakin be gama budewa ba. Wasu ruwan na sake debowa na saka kayan ci abincin mu a gaba na wanke su ma sannan na dama mata furar na saka ludayi ina ta bata tana sha a hankali har ta sha ya iashe sai na debo mata ruwa na bata ta ta sha da yawa, sai ta sauke wani irin ajiyar zuciya yana saka ni jin tausayinta fiye da da, sannan na dauke ta na maida ta dakin na fito na saka tufafinta a gaba na wanke su na shanya sannan na daw dakin kusa da ita na zauna ina ta kallonta kamar yadda ita ma take kallona irin kallo da ke nuna bata gane ni ba, ko kuma bata san inda kanta yake ba kawai dai tana gani ne. “Nana” Bata amsa ni bata kuma daina kallona ba, hakan yasa na fashe da kuka na kama hannunta na rike, na dawo amman babu kudin maganin kuma n tararda ciwonta ya fi na da, sai dai ina tunanin dawowar tawa tai amfani domin gashi yanzu ina zaune gabanta ina kula da ita. Farida ce ta shigo dakin ta tsaya daga jikin kofa tana kallona. “Bayan tafiyarki abun yai tsamari bata iya tashi komai a inda take take yinsa, na iya kokarina na kula da ita, daga baya Mama ta hanani, wacan kitchen din da ke cikin gida ya lalace shiyasa Baba ya buga mata kwano ya dawo da ita” Hannu na saka na share hawayen idonta. “Kin san ba zaki iya kula min davita yadda ya kamata ba, miyasa kika ce za ki yi? Miyasa kika bari na tafi? Aminta ba ta ce haka ba Farida yanzu da mahaifiyarki ce kina tunanin zan iya barinta a haka? Wallahi ba zan iya ba” “Na yi iya kokarina Ataa Wallahi dawainiya da Ataa ba abu ne mai sauki ba” “Eh na sani ai, ba abu ne mai sauki kula da Nana ba, ba abu ne mai sauki kula da uwar da ba taka ba, amman kin san ba dan dole ba babu yadda za ayi na tafi na barta, idan kika duba dalilin tafiyata kadai ya isa ya saka ki tausaya min ki tausaya mata ki kula da ita” Ta yi shiru bata ce komai ba, ni kuma na mike tsaye na fito waje nai alwala nai sallah na cire Hijab din na aje na rafka uban tagumi ina kallonta, ta ina zan samu mafita? Duniyar nan ta juya min ko ina na raba ba dadi, duk inda na saka gaba da zimmar cimma burina sai wani abun ya shiga gabana ya tare, sai yanzu na gane kwata kwata bana da sa'ar rayuwa kuma bana da nasara a rayuwata sai dai hakan ba zai saka na kyale rayuwar Nana a haka ba, ko da ko raina zan ransa. Ta ina zan fara baran zan koma? Ko kuwa sata zan yi? Wani zai kaiwa koke na ko kuwa mutuncina zan siyar? Duka ban gan mafita a wannan ba. Da tunanin inda zan samu taimako na kwana na a raina. ALIYU POV. Bayan sun shiga cikin gidan ne Rahma na dakinta na wuce dakinsa yai wanka ya fita masallacin unguwar yai sallah la'asar sannan ya dawo cikin gidan ya shiga dakin Rahma, zaune ya same ta saman sallaya da alama ita ta gama sallah ne a yanzu. Kasa ya zauna kusa da ita yana kallon fuskarta dake dauke da damuwa, har ya bude baki yai mata magana sai wayarsa dake aljihu tai vibration alamar kira, ciro wayar yai ganin number Mama Fulani be tsaya bata lokaci ba ya daga. “Aliyu kana ina?” “Gida” “Zo ina son magana da kai?” “Lafiya dai?” “Lafiya akan matsalar haihuwarka ne, Rahma ta fada mana gaskiya ai” “Gaskiya kuma? Wani abun ne?” Mama Fulani bata sake ce masa komai ba ta kashe wayar. Sai ya kalli Rahma “Wani abun kika fada wa Mama?” “Ban yi magana da Mama ba, amman na yi da Momy shi ma kuma ban san cewa ba su sani ba” Wani kallo ha aika mata irin kallon nan na me kika fada musu. “Na fada mata cewar matsalar haihuwar daga kai ne” “For what?” “Na dauka sun sani” “Ko sun sani be kamata ki yi wannan maganar da su Rahma” “Abun ne ya fara damuna yanzu, kuma a da suna ta ganin laifina amman yanzu za su fahimci ba daga ni ba ne wata kila za su daga min kafa” “Amman idan matsalar daga ni ne be zama damuwarki ba? Kina kokarin chanjawa daga yadda na sanki Rahma” “Ba canja nake ba Aliyu, damuwar ka damuwa ta ce, sai dai a yanzu matsalar nan ni ta fi shafuwa fiye da kai, a baki rame na ke zan iya mutuwa a ko da yaushe, ba tare da na bar abunda za a tuna da ni ba, amman kai kana nan raye har na tsawon lokaci” Be sake ce mata komai ba ya mike tsaye yana saka wayar ajihunsa ya fice daga dakin. Cikin bacin rai ya isa gidan sam be jidadin abunda Rahma tai masa ba, domin be fadawa kowa ba kuma be za ci zata iya fadawa wasu ba, wasun ma kuma iyayensa. Ko da ya shiga falon Kanensa na ciki suna ta fira da dariya, be kula su ba ya haye sama zuwa dakin Mama Fulani sai ya samu Momy da Abbah a ciki suna fira shiga dakin da murmushinsa ya zauna saman kujerar da Abbah yake zaune yana gaisawa da shi. “Abbah dawowan rana kai?” “Eh Wallahi Hajiya Fulani ta fada min na ce bari na samu na zo mu gaisa da ita” “Gaskiya kam ko mu da muke cikin gida muna wahalar ganawa da kai balle ba ko” “To ya za ayi aikin ne a haka sai hakuri” Mama Fulani ce ta shigo dakin ta tsaya jikin kofa tana kiran Aliyu. “Aliyu magana nake son yin da kai fa” Tashi Aliyu yai ya bi bayanta suka nufi dakin Baby a ciki suka zauna. Ta kalle irin duban bana wasa ba ta ce. “Rahma ta ce matsalar daga gareka ne?” “Matsalar me ba?” Yayi kamar be fahimci abunda take magana akai ba. “Ba mu da matsayin da zaka fada mana matsalar ka ne Aliyu? Ko kuma ka boye mana gaskiya ne saboda ka kare matar ka?” “Ba ko daya, na san idan na fada muku za ku damu, ni kuma ba haka na ke so ba, kuma ko da matsalar daga ni ne idan Allah ya rubuta zan haihu zan haihu” “Da gaske ne kenan?” “Gaskiya ne Mama” Mama Fulani ta rufe baki idonta cike da kwalla. “Aliyu da gaske fa ka ce” Na gyada mata kai. “Gaskiya ne Mama, sun ce kwayoyin halittafa ba su da karfin da za su rayu a mahaifar Rahma” “Kuma babu wani abun da za a iya yi? Babu wata mafita” Ta tambaya cikinnmuryar kuka domin har ga Allah bata son abunda ya taba Aliyu, balle kuma haihuwa da take babbar abu. “Mafita kawai addu'a kuma zan cigaba da neman magani ko Allah zai saka a dace” Dafe kai tai cike da tausayinsa. Tashi Aliyu yai ya koma kusa da ita ya zauna. “Mama ki daina damuwa ba komai” “Akwai komai Aliyu, haihuwa tana da muhimmanci sosai za mu so muga jikokinka, kuma ba zan so wata macen ta ki ka saboda rashin haihuwa ba” “Miya kawo wannan maganar kuma?” “Kana tunanin Rahma zata zauna da kai a haka? Gashi ta fara korafi tun yanzu, shiyasa na so ka kara auren tun tuni amman ka ki” “Babu zance aure a gabana Mama, ni bana iya zama da mace sama da daya bana iya rayuwa da mata biyu” “Ba ni kadai ba Aliyu Momynka ma ta damu kuma duk wanda yake kaunar ka idan yaji wannan maganar dole zai damu da matsalarka” “Ko wane bawa da akwai abunda ake kaddara masa Mama wata kila ni irin jarrabata kenan” “Haka ne” Ta fada tana share hawayenta sannan ta ce. “Kuma ina son na fada maka karka taba yarda ko tunanin daukar kodarka ka ce zaka bawa Rahma dan na san halinka” Murmushi yai mai sauti. “Mi ya kawo wannan maganar kuma Mama? Idan na na bata ai Rahma matata ce” “Eh matarka ce amman mu iyayenka ba ku yarda ka bata ba, kar ma ka taba wannan tunanin a rayuwarka, sai dai a nema mata magani ko kuma a samu wata dabam a siya mata amman ba taka ba sam ba mu aminta ba...” Mama Fulani bata kare gama rufe bakinta ba, Rukaiya ta shigo dakin da sallama tana fadin “Mama Abbah na kiranki” Mama Fulani ta mike tsaye ta fice tana nanatawa Aliyu zancenta, har Rukaiya ta juya zata fita Aliyu ya kirata ta juyo. “Kamal ya kawo Ataa?” “Eh amman be shigo ba ita kadai ta zo kuma Mama ta bata kudin mota ta maida ta gida” Mikewa yai tsaye da sauri. “What? Miyasa?” “Daman ai Mama ta ce ba zata kwana a gidan nan ba” Rukaiya ta bashi amsa tana kallon yadda hankalinsa ya tashi. Fita yai daga dakin ya nufi dakin Mama Fulani sai ya same ta ciki tana magana da Momy. “Mama miyasa kika kori Ataa?” Tsayawa tai kallonsa kamar yadda Momy ma take kallonsa. “Why Mama why” Ya tambaya kamar ya fasa kuka. “Aliyu wai miye alakarka da yarinyar nan ne? Ina ce a nan gidan ka santa kuka aiki kawai ta zo amman kun bi ku fitini kanku da ita” Cewar Mama Fulani Momy ta kalleta ta ce “Yanzu Fulani sai da kika sallami yarinyar nan? Ba asibiti Kamal ya kai ta ba?” “Ya dawo da ita ai na bawa Zaharadeen kudin motar ta na ce ya dora ta a mota, ni ba zan zauna da ita a gidan nan ba” “Baki kyauta min ba Mama, ba ki san kudiri akan yarinyar nan ba” Cewar Aliyu cikin rashin jindadi. “Kudirinka kamar ya?” Be bata amsa ba ya aika mata da wata tambayar. “Wace tashar kika ce ya kai?” “Ko kaje yanzu ba zaka same ta ba, and bari na fada maka indai na isa da kai karka bi bayan yarinyar nan” Mama Fulani ta fada tana nuna shi da yatsa. Sa ya zauna a saman kujerar dakin ya dafe kansa, ji yai babu dadi gaba daya ranar ba tai masa dadi ba, an kori Ataa Mama Fulani ta hana ya bi bayanta and ga abunda Rahma tai masa. “Daga zuwan yarinya ku dauki wani buri ku dora akanta yar talakawa? Abun kunya ma aiki take a gidan nan fa haba Aliyu ko kowa zai ce ya so ta ai ba da kai ba” Dagowa yai ya kalli Mama Fulani. “Ba son ta na ke ba Mama, taimakon zan yi saboda halin da muka saka ta” “Wane hali? Halin me kuka saka ta? Ina ma kasanta idan ba nan gidan ba? Ko kuwa dan fadan da nai mata da be taka kara ya karya ba shine wani hali” “Ba shi nake nufi ba, kodar mahaifiyar yarinyar nan aka cire aka sakawa Rahma ba da amincewar su ba, aikin da take a nan saboda ta samawa mahaifiyarta magani take” Momy ta zaro ido tana rufe baki. “Daman yarinyar nan ce? Ta ina ka sani?” “Ta mana aiki ai Momy ko kin manta?” Ya fada yana kallonta da damuwa a fuskarta. “Kasan da ita ce ka kyaleta tana ta shan wahala? Ka kasa taimakonta? Anya kana da imani kuwa? Wace irin zuciya ce a kirjinka? Wane irin rayuwa ce wannan?” “Momy ta ki aminta da ni ne, a duk lokacin da nai mata maganar mahaifiyarta sai ta fada min wata maganar dabam marar dadi, ta kasa yarda cewar taimakonta zan yi, a yanzu ma ina kokarin ganin ta aminta da ni ne kuma Mama ta koreta” “Innalillahi wa'inna ilaihirraji'u amman wannan yarinyar tana ganin rayuwa” Mama Fulani ta gyara tsayuwarta cikin yanayin da ke nuna bata jidadin boye mata da Aliyu yai ta ce. “Baka taba fada min wannan maganar ba, baka taba labarta min komai ba, taimakonta da kake son da ma gaskiyar abunda ya faru duk baka fada min ba” “Ba abu ne mai dadi da zan rika labartawa kowa ba Mama” “Haka ne” Ta fada sannan ya juya ta fice daga dakin. Saukowa tai downstairs ta nufi kitchen cikin wani yanayi marar misaltuwa, ko Muhseen da ke zaune a falon bata kula da shi ba har taje ta hada ma Abbah abinci ta fito ta fice ta kofar gaba zuwa part din Abbah, abincin ta kai masa ta zuba masa da kanta kamar yadda ta saba. “Lafiya dai Hajiya Fulani?” Abbah ya tambaya ganin yanayinta. “Lafiya Kalau” Bata fada masa komai ba duk kuwa da kasancewar fuskarta ta nuna hakan. Sai ya gama cin abinci ya tashi a uzurce ta rako shi har gurin mota ya shiga sannan ta nufo part dinta. Lokacin da ta shigo sai ta zauna a falo tana ta kallon su Rukaiya da Husnat dake gardama kan wani film, kallonsu kawai take amman hankalinta baya gurinsu, Aliyu ne ya sauko yana rike da wayarsa ya nufo inda Mama Fulani take zaune, sai da ya karaso daf da ita ya dan risina sannan ya ce. “Mama ina ne unguwar su yarinyar nan, kuma daga ina aka akawo miki ita?” “Ban san kowa nata ba, balle na san unguwarsu” “Amman baya kawo miki ita?” “Wacce ta kawo min ita ma ban san inda take ba” Tana fadar hakan ta mike tsaye ta nufi upstairs ta barshi a gurin risine Muhseen da sauran yan'uwnas suna kallonsa domin sun ji abunda yake tambayar Mama Fulani sun kuma fahimci wacce yake tambayar, ban da Muhseen da be san abunda yake faruwa ba. Mikewa Aliyu yai tsaye ya fice daga falon, motarsa ya nufa ya shiga ya dauki hanyar gidansa cikin damuwa. A masallacin hanya ya tsaya yai sallah magariba da isha'i sannan ya shiga gida. A falo ya fara zaunawa ya dafe kansa yana ta yawo da idonsa, har ga Allah be jidadin korar da Mama Fulani tai ma Ataa ba, all his plan yanzu na taimakonta ne and yanzu be san ma inda zai sake samunta ba, tana kadunar kamar yadda wacan ta fada masa ko kuwa tana cikin sokoto? The way da yake ganin yanayin Mama Fulani ba lallai ta fada masa inda zai ga Ataa ba. “Ban zata maganar zata haifar da wata matsala ba” Cewar Rahma tana sauko daga stairs. Kamim ta karaso Aliyu ya mike tsaye ya wuce zuwa upstairs yana fadin. “Ba shi ya dame ni ba yanzu” Juyowa tai tana kallonsa. “To me ya dame ka? Wata matsalar ce?” Be ce mata komai ba ya shige dakinsa bakin gadonsa ya zauna yana kallon dakin kamar wani bakonsa. Rahma ce ta shigo tana tafiya a hankali ta zauna kusa da shi. “Aliyu akwai wata matsalar ne?” “Yarinyar da tai mana aiki wacce aka kirewa mahaifiyarta koda aka saka miki, ta zo nan Abuja tana aiki gidan Mama Fulani and yau Mama Fulani ta koreta” Da Mamaki Rahma ta kalleshi tasan ba mutum ne mai yawan magana ba lallai ya fada mata cewar yarinyar tana aiki a gidan Mama Fulani ba, amman bata ga abun damuwa a cikin lamarin ba, akan mi zai damu da an koreta? A take zuciyarta ta soma raya mata son ta Aliyu yake. “Miye abun damuwa dan Mama fulani ta koreta? Wata kila ta mata ba daidai ba ne shiyasa ta koreta” “Ba lallai sai ta mata wani abu ba, and ba ni da wani plan a yanzu daya wuce taimakon yarinyar saboda halin da muka saka ta” “Ba mu saka ta cikin ko wane hali ba Aliyu, ba laifin mu ba ne, da muka ce a nemo siya mukai kuma ka biya kudi ba a hanya ka kareta ka cire mata kodar ba, ban ga dalilin damuwa ba sai idan son ta kake!” Ta fada da kamar fada idonta na cika da kwalla. Aliyu ya kalleta da kyau “So ne abunda ranki ya kawo miki? Ba ki yi tunanin ya kamata mu taimake ta ba? Ba ki duba irin zalincin da akai mata da irin rayuwar da ta shiga?” “Ba mu muka saka ta a cikin wata rayuwa ba Aliyu, idan ma zalinci ne b mu muka zalince ba” “Amman sanadin wa? Tun farkon da aka samu kodar nan ya kamata na bincika daga gurin wa ta fito ban yi ba, gashi abunda ya faru, yanzu kuma na gane gaskiya sai na ce zan hau gado na kwanta nai rayuwata na kyaleta? Abunda ya faru da ke Rahma ishara ce, wata kila da ba a zalinci yarinyar nan ba da yanzu kodar da aka saka miki bata kone ba” Hawaye ne ya sauko mata tana kallonsa. “Mommy ta yi gaskiya, tun ba mutu ba ka fara gajiya da ni, da ada ne baka iya yin maganar wata mace a gabana Aliyu kuma ba za fada min wata magana da zata bata min rai ba, gaskiya ne maza ba su da tabbas, korar da akai wa wata ita ce damuwarka ba lafiyata ba? Saboda ni ina daf da mutuwa ka auro wata ko?” Mikewa tai tsaye ta fice daga dakin Aliyu ya bita da ido yana jin kansa kamar zai rabe biyu, gaba daya yau komai na duniyar nan ya hade masa, rumtse ido yai gam kamin ya bude ya mike tsaye ya bi bayan Rahma, yayi zaton zai same ta tana kuka sai ya same tana hada wasu tufafin nata cikin akwati tana hawaye. Kusa da ita ya zauna yana kallon yanayinta ya kai hannu ya rika hannunta ya soma magana a hankali. “Lafiyarki ta dame ni Rahma, amman hankali ya fi karkarta akan yarinyar ina zan same ta har na taimaka mata wata kila idan na taimaka mata Allah zai dube mu ya ba mu haihuwa kuma ya baki lafiya” Mikewa tai tsaye ta nufi wardrobe ta rufe sannan ta juyo tana share hawayenta ta kalleta. “Mommy ta fada min gobe da misalin Goma na safe za mu wuce, ina son na kwanta da wuri saboda na samu bachi” Kallon kawai yake har ta zagayo ta hau saman gadon ya lullube da bedsheet ta juya masa baya. Mikewa yai shi ma ya kashe wutar dakin ya dawo bayanta ya kwanta ya rumgumeta ta baya, lumshe ido yai ba dan bachi ba sai dan tausayin Ataa daya cika masa zuciya a yanzu ya fi tausayinta fiye da Rahma, sai yanzu yake ji da ma ace Kamal be dawo fa ita ba da Mama Fulani bata koreta ba, wata kila ma ba zata iya gane hanya ba amman an tura zuwa garin be san ina take ba, maybe tai hadari ko ta gadu da wani abun be sani ba. Wannan tunanin ne ya hana shi bachi har asuba, for the first time yau ya kwanta gado daya da Rahma kuma rumgume da ita amman zuciyarsa tana gurin Ataa. Sai da yai sallah asuba sannan ya kwanta dakinsa shi kadai saboda nauyin da idonsa da kansa suke masa wai ko zai samu yin bachin da be yi ba jiya. *** *** *** A haka Mama Fulani ta kwana cikin rashin sakewa wanda ya bawa kowa mamaki ciki kuwa har da Momy da bata sake ganin walwalarta ba, gaba daya aka hadu dinning gurin cin abinci har Muhseen amman ban da Mama Fulani da ta gama shirya abinci ta koma dakinta tana karyawar. “Husna kui yi ku gama mu shirya da wuri kusan 10 jirginmu zai tashi” Momy ta fada tana mikewa tsaye ta daga dinning din ta koma falo ta zauna tana kiran wayar Aliyu dan ta tambayi jikin matarsa. Muhseen ya kalli Maryam. “Wai ina Mama?” “A dakinta take karyawa wai bata jindadi” “Ataa fa? Yau ba tai shara ba ban ma ta shigo ba, kuma tun jiya da dare na duba ganta a gareji ba ban ga kayanta ba” “Mama ta maida ita gida” Muhseen ya kalli Rukaiya da sauri wacce ke bashi amsar. “Saboda me?” “Ta gaji da ita, kuma abunda ya faru daman Mama ta ce ba zata kwanar mata a gida ba” Sai a yanzu ya abunda Aliyu yake tambayar Mama Fulani jiya har take ce masa bata san inda take ba. Jan kujerarsa yai baya ya nufi dakin Mama Fulani. Kishingide ya same ta tana cin fruit tana duba wayarta. “Mama kin kori Ataa? Mi tai?” “Ba tai komai ba, na gaji da aikinta kar kuma ka sake min maganar abunda ya shafe ta last warning” Ta fada masa sannan ta cigaba da abunda take, sai da yai kamar zai sake ce mata wani abu sai kuma yarfar da hannunsa ya juya cikin rashin jindadi ya fice daga dakin. ALIYU POV. Be farka sai sha biyu saura na rana, ya dade kwance a saman gadon idonsa biyu yana kallon silin sannan ya unkura ya tashi zaune ya sauko da kafafunsa daga kan gadon, agogon dakin ya fara kallo yana ganin sha biyu ta kusa yai hanzarin mikewa tsaye ya fice daga dakin zuwa dakin Rahma, be same ta a ciki ba sai yar takardar da ta bar masa saman gado. _Kana bachi bana son na tashe ka, Mommy ta kirani zan je na same ta a gidansu sai mu wuce see you soon_ Yana gama karanta takardar ya cikawa bakinsa iska ya busar cike da rashin jindadin yadda yau Rahma tai masa, be taba damuwa da fita ba tare da ta tambayeshi ba sai yau, yana ganin kamar ta wulakanta shi. Hannu ya kai ya dauki wayarsa da ya bari a dakin jiya sai ya ga miss calls din Momy da Husna da Maryam misalin tara da wani abu na safe kiran wayar yai sai ya ji bata shiga, hakan yasa ya kira wayar Maryam din sai ta shiga. “Hello Ya Aliyu daman Momy ce ta ce na kira domin ta yi ta kira wayarka bata shiga” “Ina Momy take?” “Ta wuce tun ten suka tashi” Ya kashe wayarsa yana fadin. “Jirgi daya suka shiga da Rahma kenan” Fitowa yai daga dakin zuwa dakinsa dan yin wanka ya shirya yaje gurin Mama Fulani, kamin ya shiga dakinsa ya kira wayar Nasir ring uku tai sannan Nasir ya daga. “Na kira wayarka baka daga ba ya jikin Rahma?” “Tana hanyar sokoto” “What ta jin sauki ne ko kuma wani ciwon ne?” “Sun sallame ta jiya, mahaifiyarta ta ce da ita za su je, and yau bata ma jira na tashi ba kuma bata tashe ni ba suka wuce” “Kun samu matsala da Rahma ne?” “Ba wani matsala kawai dai na mata maganar Ataa ne kuma taga laifina, Wallahi Nasir tunanin yarinyar nan hana ni bachi yai, Mama ta koreta tun jiya yanzu ban san halin da take ciki ba” “Garin ya miya faru?” Aliyu ya labartawa Nasir abunda ya faru sannan ya dora da. “Mama ba zata fada min inda zan same ta ba, domin jiya konda na baro gidan ranta a bace yake, amman yanzu ina son ka nema min jirgi zan je sokoto gobe, zan koma gidan nan na sake bincikawa” “Ko ba ka je da kanka ba za ka iya sakawa ayi maka Aliyu” “Yeah ina son na je da kaina ko dan Rahma” “Okay idan an gama komai zan sanar da kai” Kai ya gyada kamar ance Nasir yana gabansa sannan ya kashe wayar. Misalin biyu da rabi ya shiga part din Mama Fulani sai ya samu bata nan Baby ce kawai a gidan ita bata dade da dawowa daga scul ba. A saman Sofa ya zauna ya kira Mama Fulani a waya ringing tai sai da ta kusa katsewa sannan ta daga. “Mama na zo ba ki gida” “Eh munje gurin kamu ni da su Maryam kuma za mu shopping kamin mu dawo” “Mama ina son magana da ke” “Idan na dawo za mu yi” “Yaushe za ku dawo sai da yamma” Daga haka kai hanging wayar. Sannan ya nufi kitchen ya hadawa kansa Lipton ya sha ya fito shiga bangaren Ammy, a harabar gidan ya samu Batula tana fira da wani saurayi tana ganinshi ta sha jinin jikinta saurayin kuma ya gaishe shi Aliyu ya amsa mishi ciki ciki sannan ya wuce falon Ammy. Sai da suka gaisa sannan take koro masa da zancen tafiyar Momy. “Ko da suka wuce ina bachi, Ammy ba ki san gidansu yarinyar nan Ataa ba?” “Wallahi ban sani ba Aliyu, bata fada min ba nima dazun nake jin zancen tafiyarta gurin Muhseen yana tambaya wai ko na san inda take” Aliyu yai shiru kamar be ji ba sai kuma ya mike tsaye yana saka hannayensa aljihu dan be son Ammy taja zancen da tsawo. “Zan leka office” “To Allah ya tsare” Ko da ya fito part din Ammy wayarsa na vibration kiran Nasir na shigowa picking yai yana bude motarsa ya shiga. “Aliyu an samu jirgin da zai tashi da yamma nan zuwa Kebbi idan kana so, daga Kebbi sai ka shiga mota zuwa sokoto, domin gobe babu jirgi sai jibi shi ma kuma da safe zai tashi na san kuma ba son tafiyar safe kake ba” “Karfe nawa jirgin zai tashi?” “5 idan kana so sai a siya maka ticket” “Siya min gani nan zuwa office din ma” “Okay sai na iso” Yana kashe wayar ya shiga motarsa ya dauki hanyar kamfaninsu. Be bar kamfanin ba sai da ya rage minti talatin jirginsu ya tashi duk kuma jiran da yai na Mama Fulani ko zata dawo da wuri ne yai magana da ita dan be gane wannan fushin da ta soma yi da shi ba. Amman hakan be samu ba sai dai a waya ya kirata ya fada mata zai je sokoto tai masa Allah ya tsare. ATAA POV. Ina ta tunanin samun mafita har garin Allah ya waye, ban samu bachi ba saboda tunani da kuma nishin da Nana take yi. Bayan na gama sallah na dauki kofi naje na siyo mata koko da kosai da suga na saka mata na bata kokon kawai ta sha shima dan ina bata ne, ta ki ta ci kosan ni ma na kasa cin komai. Sai da na tabbatar ta koshi sannan na fito da ita na gyara mata jikinta na sake gyara dakim na saka Hijab dina na nufi titi, Napep na tara na hau na kama hanyar gidansu Rahma, da kudirin da ke zuciyata duk da kasancewar na san bata nan ina son naje ne na bar wa mai gadinsu sako ya fada musu domin na san ba zai rasa number da yake kiransu ba. Bakim gate din gidan Mai Napep ya aje ni na bashi kudinsa sannan na buga gate din mai gadin ya leko ya ganni sai na ga yai murmushi. “Ahh wannan na manta sunanki ke ce” “Ni ce” Na amsa masa cikin damuwa. Sai ya bude min gate din na shiga ciki. “Dan Allah so na ke ka kira matar gidan nan da mijinta a waya ka fada musu cewar akwai wata koda ta siyar idan suna so, ko kuma ka bani number wayarsu” Ya daki kirji yana kallona “Koda?” “Eh” “Ina kika samu koda?” Na yi shiru ban ce masa komai ba. “Allah yasa ba taki ce ba, kin abunda kike kuwa?” “Na sani ni dai ka kirasu kawai” “Sai dai a kira matar a waya amman Alhaji yana nan cikin gidan ai jiya da dare ya dawo” “Ba suna Abuja ba?” “Eh shi jiya da dare ya dawo bari na miki sallama da shi” Ya fada yana nufar cikin gidan. Ni dai ina tsaye kusa da gate din har ya shiga ciki sai na hango Aliyu ya fito sanye da Jallabiya daga can ya tsaya yana kallona kamin ya sauko ya doso inda nake tsaye. “Za ki siyar da koda?” Na gyada kai ina matsa yatsun hannuna. “Waya ce miki muna bukatar koda?” “Na san ai kodar matarka ta kone, dole wata za ku nema” “Saboda mi za ki siyar da kodar ki?” “Saboda na nema ma mahaifiyata lafiya” “Idan kuma ke kika mutu fa ko kika samu matsala?” “Kara ni na mutu ita ta rayu da ta muti ta barni, jiya ba tai bachi ba saboda azabar ciwo, bata iya tashi komai a inda take take yinsa bata gane kowa ni ma da nake yarta bata gane ni ba, kuma ba mu da inda za mu babu wanda zai taimaka mana ina son mahaifiyata bana son ta mutu” Na karasa cikin kuka mai karfi daman tun da na soma maganar hawaye ke sauko min. Shi ma hawayen na gani a idonsa sai yai saurin daga kansa sama ya zuba hannayensa aljihu. ZAKI By Khadeeja Candy 29... Dukawa nai a gurin saboda kukan da ya ci karfina. Sai ya bar ni a gurin ya nufi cikin gidan be dade ba sai ga shi ya fito rike da gorar ruwa da cup dayan hannunsa kuma rike da tissue, ya nufo inda nake, tissue ya fara bani ba tare da ya ce min komai ba, na karba na share hawayena sannan ya bude gorar ruwa ya zuba min a kofi ya miko min. Karba nai na sha rabin ruwan sai na risina na aje kofin kasa dana dago sai na ga ni yake kallo ba ko kyaftawa, dan kawar da fuskata nai ina goge hancina. “Ina Mamarki ta ke?” “Tana can gida” “Wane gida?” “Gidansu kawata” Shiru yai be ce komai ba har na wani lokaci idonsa na kaina ban san abunda yake kallo a jikina ba. “Shigo ciki ki zauna kamin na shirya” Yana fadar hakan ya juya da zimmar komawa ciki sai kuma ya juyo ya kalleni ganin na tsaya a gurin na ki na bi bayansa. “Ni ba zan shiga ciki ba” Na fada ina turo baki ba tare da na kalleshi ba. Matsowa yai kusa da ni sosai kamar zai hade jikinmu gabana ya shiga faduwa kamshin turarensa ya cikani sai dan matsa baya na kalleshi ido ya zare min. “Idan na ce ayi yi ake ba a min gardama, wuce ki shiga ciki” Yadda yai maganar is like yana bani umarni ne kamar wani boss. Kara tubo masa baki nai na juya sai na ji an fisgo ni da mugun karfi an juyo da ni. “Wuce ki shiga na ce” Ya fada cikin muryar dake nuna bacin ransa yana zare min ido. “Bana shiga gidan da matan gidan ba sa nan” Cikin daga murya na yi maganar har Mai gadinsa daya koma gurin gate ya zauna sai da ya kallemu. Matsowa yai da fuskarsa yana fitarda numfashi da karfi. “Haka Muhseen yake miki ko? Shiyasa kike dauko ko wane namiji dan iska, mahaukaciya kawai” Yana fadar hakan ya sake ni da karfi har yana ture baya kamar zan fadi, sannan ya juya ya koma ciki ya bar ni a gurin tsaye. Juyowa nai na dawo gurin mai gadin na ce masa. “Dan Allah ka kira matar gidan ka fada mata yanzu” “Ba kun yi magana da shi ba?” “Be ce min komai ba sai bakin fada, ni dai dan Allah ka kirata” “Wallahi Alhajin ne ba a iya masa yanzu zan iya kiranta ya zama ganin laifi” Na marairaice masa fuska tare da dukawa kasa ina rokonsa. “Ka taimaka min dan girman Allah, Wallahi ina cikin matsala sosai” “Gaskiya tun da ya nuna ba ya ra'ayi kara ki hakura kawai, ko kuma na baki number ta kina da waya?” “Ba ni da waya Wallahi amman dan Allah ka taimaka min” “Zan kirata amman sai mai gidan ya fita, domin ni bana iya magana kadan idan kuma nai karai ya ji zai iya korata dan ya fada min baya son hayani” “In tafi zaka kirata kenan?” “Eh zan kirata In-Sha-Allah” Daya bani tabbacin zai kirata ne yasa na taso na fito daga gidan, cikin rashin jindadin domin haka ta bata cin ma ruwa ba, daman nasan indai shi ne za ko zai siya sai ya wulakantani tunda dan wulakanci ne. Har na kama hanya sai kuma ya juya na koma saboda bacin ran daya same ni gate din gidan na buga da karfi mai gadin ya sake leko ganina ya bude min karamar kofar. “Dawowa kikai?” “Eh” Na fada da kamar Fada sannan na wuce zuwa bakin kofar falon na taka na kai jikin kofar na buga kofar da karfin tsiya. “Eh daman ai na san ba zaka siya ba, amman idan ta zalince ce kana so ko? Idan a hanya ka hadu da ni zaka iya sakawa a danne a min tiyata a cire a sakawa shegiyar matarka, mugu kawai duk halin da mahaifiyata ta shiga kai ne sanadi kuma ba zan taba yafe muku ba azzalumai masu.... ” Ban karasa ba ya bude kofar falon sai nai shiru na kawarda fuskata ina hawaye. Farin jean ne jikinsa da bakar riga mai kwalliya sai fararen takalmi hannunsa rike da waya da kuma keys din mota, kamshin turarensa duk ya cika gurin shi kuma ya min fadi a ido tsoronsa ya cika zuciya, ba kuma tsoro na kar ya dake ni ba, yana da wani irin kwarjinin da ke saka mutun tsoro na rashin dalili. Yana tsaye jikinnkofar daga ciki ni kuka ina daga waje kaina na wani gafen shi kuma idonsa a kaina kamar yana hararata kuma ba harararba. Juyowa nai na sauko daga gurin na nufi gate na fice abuna ba tare da na kara cewa komai ba, shi ma kuma be ce min ba, hanya na biyo ina ta tunanina kala kala ciwon nana neman maganinta da kuma abunda mutumen nan da matarsa suka min. Da karfi aka faka mota gabana sai na ga an turo ganbun motar an bude shi, dana leka sai na ga Aliyu ne a ciki yana kallon wani gurin, ba zai iya cewa na shigo ba saboda bakin girman kansa, idan ma na shiga ban san inda zai kai ni ba, sai akwai nai gaba abuna na barshi a gurin. Sai ya kara cin gabana da motar ba tare da ya min magana ba nima na kara yin gaba abuna, sai ya fito daga cikin motar ya biyo bayana ya fisgo kafadar hannuna ya dawo da ni ya saka ni da karfi a front seat ya rufe motar ya zagayo gefensa ya shiga ya hau titi ba tare daya kalleni ba. “Wallahi ni ba zan yarda ka cutar da ni ba, wacan zalincin da kuka mana ya isa cin amanar da muka min kai da Mama Fulani sai Allah ya saka min” Na fada ina saka dayan hannuna na murza inda ya rikani cikin kukan dana fara tun a lokacin daya rikoni ya saka ni motar domin ba karamin riko yai min har yanzu ina jin ciwo a guri. Wayarsa ya ciro ya shiga wani guri yai dannen dannensa sai na ji karar kiran waya yana fita ta speakers din motar. “Hello Ranka ya dade idan ka kira ta samu, idan ba ta samu ba sai dai mu kira mu gaishe ka” “To ta samu Bukar kana ina?” “Ina gida tare da iyalina” “Ina da patient ne ambulance nake so” “Subhanallahi waye ba lafiya?” “Baka santa ba” “Wani guri zan saka a turo maka yanzu” Sai yai shiru be ce komai ba, ni yake jira nai magana ni kuma ban sammaci hakan ba tun da naga ko kallona be yi ba. “Ko ba ki ji ba?” Ya fada still be kalleni. “A Clapperto road house number 11 amman ta bayan gidan zaka shigo kananan gidanjen da suke nan” “Okay” Yana fadar hakan sai Aliyu ya katse kiran ya dauki wani farin Bluetooth ya saka a kunnesa ya kara gudun da yake. Cikin kannnen lokaci muka isa Clapperto road, wani abun mamaki har kofar gidansu Farida ya faka motarsa ina ta mamakin yadda akai ya san gurin kai tsaye ba tare daya tambaye ni ba. Fita nai daga motar na nufi dakin na kwano ba tare da rufe masa motarta ba. Wasu tufafin na canja mata na saka mata Hijab, sannan na zauna kusa da ita tana ta kallona kamar bata gane ni ba har yanzu. Ina jin lokacin da motar asibitin ta tsaya sai na ji muryar maza biyu sun doso dakin kwanon da muke ciki. “Ina marar lafiyar take?” “Gata nan” Na fada da sauri ina mikewa tsaye sai suka shigo suka dauki Nana suka fita da ita zuwa cikin motar asibitin Farida da Mahaifiyarta suka fito suna kallo har da wasu makota da ke kusa. “Ni ina zan shiga?” Na tambayi mutanen da suka shige cikin motar. Sai na ji muryar Aliyu yana fadin. “Nan za ki shiga” Da sauri na nufi motar na shiga daman ban rufe ba, shi ma kuma jin kai ya hana shi rufewa. Da na shiga motar sai yai mata keys muka bi bayan mutane sai da muka fara nisa sai na ga sun bi hanyar Uduth shi kuma ya dauki hanyar arkilla da ni. “Kai ba fa ita za a cirewa koda ba ni, ita ba kasa an cire mata daya ba, idan aka kara cire wannan mutuwa za tai” Na fada ina shirin fashewa da kuka. “Karki sake min maganar kodar nan karki sake” Shine Kawai abunda ya fada min ba tare daya kalleni ba ya cigaba da tukinsa ni kuma na cigaba da rare masa kukana har muka isa arkilla, wata hanyar ya biyo inda manya gidaje na alfarma, bakin wani katon gate ya tsaya wanda saman gate din duk iccen fulawa ne da yai rassa ya sauko har gurin gate din. Da karfi zai saka a cire min kodar ya sakawa matarsa ni ya kyale ni shine kawai abunda zuciyarta take raya min. Da muka shiga harabar gidan sai na ga manyan motoci uku a fake kusa da ta farkon ya faka tashi motar ya bude ya fita ba tare da ya ce min komai ba. Nima na bude na fito na tsaya gurin motar ina hawaye gaba daya tsoro ya gama kamani dan a nawa tunanin wata kila ma tsafi yake. Da kai yai min alama da na wuce ciki ni kuma na lake kafadata ta alamar ba zanje din ba, gaba yai abunsa ya bar a gurin ina karewa gidan kallo ina hawaye, gidan be min kama da na yan yankan kai ba amman ba ni da tabbacin ba cutar da ni zai yi ba, gashi kuma ya saka an tafi da Nana waya sani ko sani abun za a mata. Karar bude kofar falon naji kamar yadda na ji lokacin da zai shiga, sai na hango wata farar mace ta fito daga falon ta doso inda nake tsoro ne ya kamani a zatona wani abun zata min sai ta kusan karasowa kusa da ni sai na ga ashe matar da na taba gani gidan Mama Fulani ce wacce ta ba ni cake, fuskarta da tausayi ta karaso inda nake ta kai hannunta ya rika fuskata sai na ga idonta da hawaye. “Alhamdulillah Allah mun gode maka, sannu kinji” Na gyada kai ina hawaye sai tasa hijabina ta goge min fuskar. “Daina kuka kinji zo muje ciki” “Ina nan ya kawo ni?” “Ya kawo ki inda za ki samu gata ki samu jindadi a nuna miki kauna” “Mamana tana asibiti ya saka an tafi da ita ban san abunda zai mata ba, bana kwanciyar hankali har sai naji halin da take ciki” “Ba cutar da ita zai yi ba, shi ma ya dade yana nemanki da inda kike ni da shi, ban san cewa ke ce ba sai bayan da Fulani ta koreki, ki aminta da mu Wallahi ba za mu cutar da ke ba” “Mahaifiyata fa?” “Ita ba zai mata komai ba” Matar ta fada tana hawaye sai ta rumgume ganin ina kuka. Shi kuma ya fito daga falon ya nufo inda muka na yi zaton ko wani abun zai fada min sai na ga ya bude motarsa ya shiga. “Dan wajen Fulani komai ake ciki ka kira ni saboda hankalinta ya kwanta” “Okay Momy” Ya fada yana kallona daga cikin farin gilashi motar. Sannan taja hannuna ta nufi hanyar falon da ni, da muka shiga ciki sai sai yan matan nan da na gani idan Mama Fulani su Biyu Siyama da Husna da kuma wata wacce ban sani ba suka ce min “Sannu” Kai kawai na gyada musu na zauna a kujerar da matar ta zaunar da ni. Sannan ta zauna kusa da ni ta rike hannayena. “Dan Allah ki daina kuka Wallahi raunana min zuciya kike idan kina kukan nan sai ki saka nima nai” Sai kuma ta kalli Siyama tana share hawayenta ta ce. “Shiga ciki ki hada mata ruwan wanka” “Aa ba zan yi wanka ba, na fi son naje asibitin kusa da ita hankalina zai fi kwanciya” “Za a kula da ita za a mata duk abunda take bukata idan ma kinje ba wani abun za ki mata ba, kuma ba cutar da ita zai yi ba taimakonta zai yi” Kai na girgiza. “Aa ni ban yarda ba, wacan karon ma cewa aka yi taimakona za ayi ashe koda za a cire mata a bar mu da lalura, kuma mutanen da sukai wacan aikin sune a yanzu, a gabana ya kira wani likita ya aiko da mota aka tafi da ita ni kuma ya kawo ni nan, hankalina be kwanta ba, zai iya cirewa ya sake kasawa matarsa, dan girman Allah ku tauyasa min ba ni da kowa a duniyar nan sai Nana ban san kowa ba a cikin danginmu Wallahi idan ta mutu ban san inda zan je ba” Ina rufe baki matar ya saka a kirjinta ta rumgume ta fashe da kuka sautin kukanta har ya fi nawa dagawa. Husna da bakuwar da ban san sunanta ba suma suka saka kukan dakin yai tsin ba ka jin komai sai sautin kukan mutane hudu, ni Matar, Husna da bakuwar ban da Siyama da ita hawaye kawai take. Mun dauki lokaci muna kuka duka aka rasa wanda zai bawa wani hakuri balle kuma har ya rarrashi, Siyama ce ya shiga daya daga cikin dakunan ta hada ruwan wankam sannan ta fito tana fadin. “Momy ga su can na hada dakina” “To” Wacce aka kira da Momy ta amsa cikin muryar kuka, ni dai ina rumgume a kirjinta ina fitarda numfashi a hankali, na jidadin rumgumar da tai min rabon dana kwanta jikin Nana a haka har na manta amman yau wata uwar ta rumgume ni na yi kuka a jikin rigarta ba tare da ta nuna min kyama ba. Ko da yake ba a fuska da hali ake gane mugun mutum da na kwarai ba, domin da a fuska ne da Doc Asim be mana haka ba, daga nai daga jikinta ina jan majina sai ta sauke ajiyar zuciya ta ce. “Ta so mu shiga ciki ki yi wanka” “Momy bari na kaita mana” Bakuwar ta fada tana mikewa tsaye gaban tv dana tarar da su suna game ta nufo inda nake, wata kila ita ma yar gidan ce domin ta yi kama da Momyn sosai. Hannuna ta rika na tashi tsaye taja har cikin dakin dan madaidaici mai gado daya da yar karamar kujera da teburin karatu an kawata shi iya gwargwado. “Nan za ki cire kayanki ko sai kin shiga ciki” “Ciki zan cire” Ta min murmushi. “Ya sunanki hala?” “Aisha” “Ni kuma sunana Amina, jin ga a girme na girmeki dan haka ke kanwata ce” Bance mata komai ba sai ta nuna min bandakin. “Shiga ciki sai ki yi wankan bari na kawo miki wasu tufafin da za ki saka” “To” Na nufi bandakin cikin tsoro domin ni har yanzu zuciyata bata natsu da su ba, a dayan bangaren kuma na kasa aminta cewar Aliyu ba cutar da Nana zai yi ba. Ban wani dade gurin wankan ba na gama na dauki zanena na daura na fito tsoron gashina har gadon bayana. Ko da na fito Amina tana zaune rike da kayan tana jirana. “Wow” Ta fada tana kallona sai kuma ta aje kayan hannuna ta nufo bayana tana taba gashina. “Ke da gaske gashinki ne? Innalillahi wa'inna ilaihirraji'u, kamar aljana ko dai kari kikai” “Gashi na ne” Na fada cikin rashin sakewa. “Ki shafa mai ki saka rigar” Ta fada tana fita daga dakin. Abaya ce yellow da under wears sai dan karami dankwali baki. Sai da na fara saka kayan ciki sannan na saka abayar na daura dankwalin a fito da tsorona sai na zauna kasa, gudun kar na zauna a saman gadon ya zama laifi komai ban shafa ba duk kuwa da tulin kayan kwaliyar da suke dakin tsoro nake ban sani ba ko suma kamar Maryam da Rukaiya suke. Kofar dakin aka turo sai ga Momy ta shigo dauke da plate da kofi. “Aa ya kika zauna kasa? Tashi ki zauna saman gadon mana” “Nan din ma ya ishe ni” “Aa tashi ki zauna ya za ki zauna kasa” Saman gadon ta aje plate din da ke rufe sai ta mika min kofin hannunta ashe tea ne a ciki. “Ki ci abinci kinji ki kwantar da hankalinki ki yarda da mu ba zamu taba cutar da ke ba, kuma mahaifiyarki zata samu lafiya ta warke In-Sha-Allah” “Bana jin yunwa bana iya cin komai a yanzu” Na fada ina aje kofin tea a kasa sai ta dafa ni ta zaunar da ni kusa da ita saman gadon. “Na sani an miki zalinci kuma an miki rashin kyautawa, tabbas Dan wajen Fulani ya yi kuskura ban sani ba ko za ki yarda cewar ba da saninsa aka aikata miki hakan ba?” “Idan ba da saninsa ba ya za ayi a sakawa matarsa? Kawai sun yi amfani da rashin ilmina ne suka saka na saka hannu a takardun da sunan taimakona za ayi ashe kodarta za a cire, saboda ya tambayi ne na ce masa ba ni da kowa sai yai amfani da wannan damar ya cire mata koda kuma ya saka a kulleni har kwana hudu gidan yan sanda, wai na bata masa suna” Na karasa ina hawaye. “Wallahi ba da wanin sanin sa akai miki haka ba, kudi aka bashi aka ce ya siyo ba mu san cewa zalinci zai yi ya cire kodar mahaifiyarki, kuma tun daga lokacin da abun ya faru muke ta neman ki da inda za mu ganki mu taimaka miki amman ba mu samu ganinki ba, ban san cewa ke ce kike aiki a gidan Fulani ba sai daga baya, shi kuma ya fada min cewar kin ki bashi hadin kai ne shiyasa be taimaka miki ba” “Ina tsoron taimakon kowa ballanata na shi, Wallahi Aliyuna nan bashi da imani da tausayi kansa kawai ya sani” Wasu yawu ta hade da karfi tai min murmushi. “Ba ki fahimce shi bane, amman za ki sanshi nan gaba kadan” Ban sake cewa komai ba bayan hawayena da na share ina murza yatsun hannuna na rasa yadda zan yi zuciyata ta aminta cewar ba cutar da nana Aliyu zai sake yi ba. ALIYU POV. Daga Arkilla ya koma uduth din, duk wani abu da ake ma patient kamin a shiga da shi ganin likita shi yai kama daga karba kati da kaiwa a bude file. Sannan ya kira Doc Bukar ya fada masa cewar ya kawo ta har an shiga da ita ciki, ba bata lokaci Doc Bukar ya iso asibitin sai da Aliyu yai masa bayanin cewar matsalar koda ce sannan ya shiga dakin da aka kaita ya soma bata taimakon gaggauwa shi da wani likitan. Bayan sun fito Doc Bukar ya saka wasu nurses din suka kaita akai mata hoto a aka debi jininta sannan ya canja mata daki aka kaita wani dakin na musamman. “Aliyu ya akai aka bar matar nan haka? Ciwon nan yana kokarin cinye ta?” Lokacin da suka jero suka fito daga emergency ne Bukar ke masa wannan tambayar. “I can't tell yanzu fada min ba zata samu sauki ba?” “Zata samu mana, amman dole sai mun jira Doc Muhseen ya zo shi kadai zai mata aikin nan tun da Doc Mustapha yana waje, daman sune likitocin da suka fi kwarewa wannan fannin” “Ka kira shi?” “No na yi request a kira shi dai, ai ba mu muke kira ba, kuma ko bayan nata ai zai zo ya duba wasu patients daman amman sai next week” “Kana tunanin zata kai gobe?” “Yes zata iya kaiwa next year ma a haka, daman yanzu jini da ruwa ne abunda ta fi bukata, to mun saka mata ruwa jinin kuma na saka a bincika idan kawai wanda yai daidai da nata ko kuma zai iya zama a jikinta” “Ka gwada nawa mana idan zai yi” Doc Bukar ya kalleshi. “Seriously?” “Yes ina son rayuwar matar nan Bukar, ko me za ayi dai i need her alive” “Then ka kira dan uwanka ka fada masa idan zai iya ya zo ya duba ta yau ma, idan yai mata aiki ina da tabbacin nan da two weeks zata koma normal” Wani guntun numfashi Aliyu yaja ya sauke sannan ya kalli Doc Bukar din ya ce. “Muje a gwada jinin” Tare suka juya suka zuwa lap a can aka gwada jininsa da na Nana aka ga zai shiga sai ya kwanta aka cire gora uku a jikinsa aka sannan ya taso ya fito Doc Bukar ma bashi gangon madara. “Ya jikin Rahma tana ta samun sauki dai ko?” “Ka ji bata da lafiya ne?” “Yes ba mahaifinta ya saka cigiya gurin likitoci cewar yana bukatar kodar siyarwa ba, sai dai samun koda yanzu ba abu ne mai sauki ba ba kowa ke iya siyarda wani bangare na jikinsa ba, kamar wannan maybe ita ta siyar muku da na farkon gashi yanzu sai an sake mata aiki” Sai da Aliyu ya shaye madarar sannan ya jefar da gongon ya kalli Doc Bukar kamar zai yi magana sai kuma yai shiru dan yasan daya fadi gaskiya kara ma kawai yai shiru dan babu wanda zai yarda cewar ba da amincewar Doc Asim ya cire kodar ba. “What is better now is ka kira Muhseen ka fada masa cewar kana da patient ya zo ya duba maka ita, na san zai yi ai” “Zan kira” Ya bashi amsa sannan ya rako shi har gurin motarsa ya shiga ya sannan Doc Bukar ya juya ya koma cikin asibiti Aliyu kuma ya amsa wayar da Rahma take masa. “Aliyu ka shigo garin nan?” “Eh” “Amman ban sani ba” “Shigowar dare nai, ya jikinki?” “Aliyu yarinyar nan ka biyo ko?” Yayi shiru be ce mata komai ba. “Aliyu wai ba zaka fita harkar yarinyar nan ba? Shikenan daga yarinya ta zo tayi karya kai kuma ka zauna akai ka yarda cewar hakan din ne?” “Babu ruwanki a cikin lamarin nan, ban nemi shawararki ba akaran kaina nake komai, and bana son yadda kike min magana kamar kina saka ni nai dole” Ajiyar zuciya ta sauke daga can cikin wayar sannan ta dora da dalilin daya saka ta kirashi. “Adamu mai gadi ya fada min wata ta zo zata siyar da kodarta kuma ka yi magana da ita ina take?” “Ataa ce yarinyar da kike fada akanta, ta zo ta siyarda kodar dan kawai ta nema mahaifiyarta magani irin wannan yarinyar ce kike cewa kar a taimakawa? Haba Rahma” Kashe wayar tai bata sake cewa komai ba, shi kuma ya sauke yana mai jin haushin abunda tai masa dan shi ba a kashe nasa waya sai dai shi ya kashe maka indai ba Momy ba ko Mama Fulani ko Abbah Daddy, sai ko Nasir shi ma kuma ba kullum ba. Sai ya tuka motar ya dauki hanyar gidansu Rahma dan zuwa ganinta and yana son yin wasu maganganun da ita, a dayan bangaren kuma yana jin kamar ya kira Muhseen yai masa magana, duk da yasan ba abune mai sauki a gareshi ba kiran Muhseen har yai requesting wani abu a gurinsa, he can't remember when last yai waya da shi, wani bangaren na zuciyarsa yana fada masa ya hakura kawai har sai next week idan Muhseen din ya zo, sai kuma yaji kamar ba zai iya kyale Nana a cikin wannan halin ba bayan sune silar shigarta halin kuma yana da yadda zai yi. Cikin wayarsa ya shiga ya nemo number Muhseen yana ta kallonta kamar ba zai kira ba, sai kuma sata zuciyar tace masa ya aika masa kawai da sako, wata kila kuma kiran ya fi dan zai fi daukar abun da muhimmanci, ba shi da wani zabi daya wuce kiran idan ma ya koma gida be san ta yadda Ataa zata dauki abun ba idan ya fada mata likitan da zai mata aiki sai next week zai zo wata kila ba zata yarda da shi ba. Ringing tai har ta katse Muhseen be dauka ba, bs karamin jihadi yai na sake kiransa tare da alkwarin idan har be daga ba ba zai sake kiransa ba, tana yin ringing daya Muhseen ya daga. “Ya akai?” Aliyu yai shiru na wani lokaci ba tare da yace komai ba tana jin zafin tambayar da Muhseen yai masa. Har Muhseen zai kashe wayar sai Aliyu ya ce. “Akwai wata patient mai matsalar koda, ina son ka duba ta gobe” “Yaushe ka zama ogana ne da har zaka ba ni umarni?” Aliyu yai shiru be ce komai ba sai dantsar hakora yake gumi na karyo masa a take. Can Muhseen ya ce “Idan ma wani abun ne ai ba kai zaka fada ba, daga can asibitin za a turo min mail, sai idan alfarma kake nema then say it” A fusace Aliyu ya katse kiran ya gwammace yai hakan da ya furta neman alfarma a gurin kowa balle kuma Muhseen da furta hakan zai ba shi damar ganin ramarsa. Bacin ransa ne ya saka yaji ba zai iya zuwa gurin Rahma a haka ba, can din ma yasan ba bacin rai zai kwaso domin ba fahimtarsa zata yi ba. Canja hanya yai ya dauki hanyar da zata sadashi da Arkilla phone dinsa a dayan hannunsa yana driving da dayan, sako ya shigo wayarsa ta saman screen din ya karanta abunda Muhseen ya turo masa. _Ka fara bawa Ataa wayar zan yi magana da ita then zan zo gobe_ Wani murmushin haushi Aliyu ya buga wayar a front seat yana wani irin huce how on earth Muhseen zai saka masa doka wai sai ya bawa Ataa ya yi waya da ita sannan zai zo, har ya isa gida be daina jin zuciyarsa na tafasa ba. A harabar gidan ya samu Momy zaune tana gyara giďa daman ta kan zauna wani lokacin har ita da Daddy ko da yara, tana ganin yadda Aliyu ya fito mota tasan akwai bacin rai a tare da shi, kai tsaye inda take zaune ya nufo ya zauna kusa da ita. “Wai ni Muhseen zai sakawa doka?” “Miya faru?” A nan ya labarta mata abunda ya faru sai Momy tai murmushi. “To yanzu kiran waya ka bata su yi magana shine wani abu?” Yayi shiru be ce komai ba. Momy ta dauki wayarta ta kira Siyama tace ta fito tare da Ataa su same ta harabar gidan, a tare suka fito Siyama da Ataa sai dai Ataa ta fi sauri gurin karasowa gurin domin a tunaninta wani abun ne. “Miya faru? Ina Nana” “Waya za ki yi da Muhseen yanzu, shi zai zo ya duba Maman ki gobe” Momy ta fada tana kiran Muhseen din waya. Sai da suka gaisa sannan ta ce masa. “Ga Ataa din” “Momy ba a wayarki na ke son magana da ita ba, a wayar Aliyu” “Naga kamar duka daya ne ai” “Na sani Momy amman wayarsa na ke so please” Katse kiran Momy tai ta kalli Aliyu. “Da wayarka yake son magana da ita, ka kira shi yanzu nan ka bata” Har ya bude baki zai yi magana sai Momy ta tari numfashinsa. “Umarni ne ka kira shi ka bata wayar ta ce” Ta fada da kamar fada tana kallonsa fuskarta babu alamun wasa. “Wayar tana mota” “Je ka dauko” Tashi yai ya nufi motar ya bude ya dauko wayar ya dawo ya zauna sannan ya kira Muhseen ya mikawa Ataa wayar. Bata karba ba ta tsaya kallonsa sai ya daka mata tsawa. “Ki karba mana...!” A razane ta mika hannu biyu ta karba idonta na kokarin cika da hawaye ta kara wayar a kunne. “Karka sake daka mata tsawa balle kuma ka ce zaka nuna nata dan yatsa, bata jidadi a wani gurin ba ba zaka zo nan ka hana ta ba, abunda kake yi ma kannenka da kowa ita ba zan daukar maka ba” Momy ta fada tana nuna shi da yatsa cike da jin haushin yadda ya razana ta sannan ta mike tsaye ta dauki gyaďarta ta bar masa gurin, dafe kansa yai a gurin har yanzu gumin bacin rai ne yake sauko masa. Gaisawa Ataa ta fara yi da Muhseen cikin sautin kuka sai ya ce. “Mi aka miki kike kuka?” “Ba a min komai ba” “Zan zo na duba Mamanki gobe kina so?” “Eh” “To zan zo, ki kula da kan ki kinji? Idan na zo za mu yi magana da ke” “To” Daga haka ya kashe wayar, sai ta mikawa Aliyu wayarsa. “Gashi” Dagowa yai ya kalleta kamin ya kai hannu ya karbi wayar ya buga ta da kasa iya karfinsa a take wayar ta watse Ataa kuma tai ihu tai baya a zatonta wani abun zai mata. *ZAKI By Khadeeja Candy 30... Daga gidansu Rahma gidansa ya dawo, sai ya tsaya a cikin mota ya kwantar da kujerar baya ya kwanta hannayensa rumgume a kirji. Gaba daya wunin yau be masa dadi ba, tun da yake a rayuwarsa be taba samun kansa ciki matsala irin wannan ba. Rahma a gafe ga Ataa and now Muhseen, sai a yanzu yake nadamar sanar da Momy abunda ya faru tsakaninsa da Muhseen da bata cilasta masa ya kira shi ba, da ransa be bace kamar haka ba. Ya dade a zaune cikin motar sannan ya bude ya fito ya shiga cikin gidan kai tsaye dakinsa ya wuce, ya kwanta be tashi ba sai kusan sallah magariba, tufafin jikinsa ya cire ya shiga bathroom yai wanka tare da alwala ya fito ya sake shiryawa cikin wasu tufafin ya feshe jikinsa da expensive perfume sannan ya fito ya sake shiga motar ya dauki hanyar gobirawa, a masallacin unguwar ya tsaya yai sallah kusa da wani mai siyardar nama, bayan ya gama ya shiga wani babban shago ya zabi waya mai tsada ya biya da ATM dinsa sannan ya fito ya shiga motarsa a cikin motar ya fiddo wayar ya kunna sannan ya soma driving da hannu daya. Har ya isa family house dinsu Arkilla, kusa da inda ya fasa wayar ya faka motarsa ya sauke gilashin motar yana kallon yadda wayar ta watse, da duhun magariba amman ko'ina haske ne kamar rana, ya dade yana kallon gurin sim dinsa da memory yake son cirewa ya saka a wannan wayar amman baya son taba wayar gaba daya ta fice a ransa. Fita yai daga motar ya nufi kofar falo ya shiga, Siyama kawai ya samu a ciki tana kallon rawar babban yaro a plasma tana koyon yadda suke, sai dai ganin Aliyu ya saka ta saurin zaunawa tare da canja channel din da take kallo zuwa wata dabam. “Sannu da zuwa Ya Aliyu” Sai da ya karewa falon kallo sannan ya ce. “Ina Ataa da Husna?” “Ataa tana asibiti Husna kuma sun fita ita da Anty Amina Momy ta aike su” “Waya kai Ataa asibiti?” “Kuka tai yi shine Momy ta saka Anty Amina ta kaita” “Je waje ki dauko min sims dina da Memory” Shine abunda ya fada sannan ya nufi dakin mahaifiyarsa, zaune ya samu Momy gaban madubi tana cire gulagulan hannunta, a gafen gadonta ya zauna yana cirewa wayar murfi, bata ce masa komai ba har Siyama ta shigo ta kawo masa sims din da memory ya karba ya saka a wayar sannan ya kunna. “Ga abincin dare can zaka je ka kaiwa Ataa asibiti” Momy ta fada bayan Siyama ta fice daga dakin. “Momy ba za a bawa Siyama ko Amina ta kai ba?” “Kai na ga dama, ka ce kana son taimakawa yarinya amman kana kokarin bata kanka a gurinta, wata rayuwa kake daukarwa kanka wace zata kara saka yarinyar ta tsane ka kuma ta yarda cewar da hadin bakinka aka cutar da ita, fasa waya a gabanta daka mata tsawa, ko zare mata ido ba ba zai kara maka komai a gurinta ba sai tsana” “Ba saboda ita na fasa waya ba” Ya bata amsa yayinda yake kunna wayar. “Saboda Muhseen ko? Kana jin cewar ka ragu saboda ka kira Muhseen ka bata sun yi waya right? Shi bata waya suyi magana wani laifi ko abun jin zafi” “Momy Muhseen kanena ne, be kamata yai min haka ba” “Shikenan dan yana kanenka ba zai iya cewa ka kaiwa wani yai waya da shi ba? Wannan wane irin jin kai ne da kai haka?” Yayi shiru be ce komai domin yana tunanin duk abunda zai fadawa Momy ba fahimta za tai ba, Mama Fulani ce kawai take fahimtarsa har ta goya masa baya, kuma bata taba masa magana akan wannan ba. “Zaka je ko na tashi naje da kaina” Dagowa yai daga kallon wayar da yake ya kalli Momy wacce ta daure fuska. “Zanje Momy amman kamar kina fushi da ni, kuma kin san ina damuwa idan ke da Mama kuka fushi da ni” “Bana jindadin yadda zamantakewar ku da Muhseen yake sam, ita ma kanta na san ba dadi take ji ba, tana kyale ku ne kawai saboda babu yadda za tai” “Momy matsalar ba daga ni ba ne daga Muhseen ne ya cika son shiga rayuwata ne kawai” “Ka gani ba, wannan halin na ka shi yake bashi haushi yake ba kowa ma haushi, kai baka taba yarda cewar ka yi laifi ba, baka tana yarda ace kaine mai laifi sai jin kai da son wulakanta kowa, babu abunda ka rage a halin Fulani kuma Wallahi wannan dabi'un ba su da ce da kai ba” “Momy kawai kina son ganin laifina ne ki bawa Muhseen gaskiya bayan shi ne yake abunda be da ce” “Na sani wani lokacin yana yin abunda be dace ba, amman ka fi zurfafa sama da shi, and dole na bawa Muhseen gaskiya na kare shi kamar yadda nahaifiyarsa take maka, ba zan taba yarda ka ce zaka ciwa danta mutunci ba ko ka wulakanta shi ba, ku rika abu kamar ba yan'uwan juna ba, kana ikirarin kai babba ne amman baka iya kawar da kai daga ganin wani abun ka  ka kyale?” Kansa ya mayar gurin wyar yana ta taba ba dan kuma yana bukatar tabawarba sai dan be san abunda zai cewa Momy ba, har tai fadanta ta gama ta fice daga dakin be ce gama be sake cewa komai ba. Bayan ajiyar zuciya daya sauke ya fito daga dakin ya nufi dinning inda Momy take hada kulolin abinci da kwadon da saka plate a ciki da spoon ta mika masa. “Idan ka je kuma ka daka mata tsawa idan bata karba ba” Murmushi yai ya karba ya nufi kofa Siyama kuma ta dauki ragowar kulolin ta saka masa a mota har ta juya zata koma ya kirata. “Shigo muje idan munje can za ki rika kayan” “To” Ta fada tana bude front seat ta zauna shi kuma yai ma motar key suka kama hanyar asibitin. A inda ake faka motoci ya faka motarsa sannan bude motar ya fito ya bude gidan baya ya dauki kwandon plate din da karamar kula Siyama kuma ta riko mayan kulolin guda biyu ta dora daya saman daya. Security din na ganin zubinsu ya san ba irin zubin mutanen da zai tarewa kofa ba ne, da kansa ma ya bude musu ward din Anas room suka shiga. Aliyu ne a gaba domin shi ya san inda dakin yake Siyama na biye da shi a baya har suka isa cikin dakin.   Tura kofar kawai yai ya shiga ba tare da sallama ba, sai dai yana kokarin sakin fuskarsa duk da ba murmushi yake son yi ba. Zaune ya samu Ataa saman gadon da mahaifiyarta take kwance tana bachi, Doc Bukar kuma na zaune saman kujerar da ke fuskartar Ataa yana nuna mata abu a laptop dinsa, babu Hijab a jikinta sai dankwali gashin kanta a waje ta rike shi tana wasa da shi tana kallon video a laptop. Haka kawai sai Aliyu ya ji babu dadi samun su haka, baya son ganin Ataa da wani namijin a yanzu dan gani yake kyaunta zai iya jan hankalin wani namijin ya cutar da ita. Duk yadda yai kokarin sakin fuskarsa sai zuciyarsa tai masa ba dadi. Kusa da Doc Bukar Siyama ta aje kulolin hannunta sannan ta karbi na Aliyu ta aje kasa, da gangan Aliyu ya kasa cewa Doc Bukar komai sai kokarin danne bacin ransa yake. “Aliyu ka shigo” Doc Bukar ya tambaya yana rufe laptop din da murmushi a fuskarsa. “Eh” Mike tsaye Bukar yai yana fadin. “Ka yi waya da Muhseen din?” “Na yi” Yadda Bukar yaji Aliyu na amsa masa magana da a take kuma babu sakewa ya san ransa ne a bace sai dai be yi zaton ganinsa da Ataa bacin ran nasa ba, a zatonta wani abun ne dabam yake damunsa. “To ni zan wuce yar Fulani sai jango ko?” “To sai da safe” Ataa ta fada murya kasa kasa shi kuma ya juya ya fice yana murmushi. Duka duka yaushe aka Ataa ta zo asibiti da har zata sake da Doc Bukar haka shine abunda ya tsayawa Aliyu a rai. “Ina Hijabin ki?” Ya tambaya da kamar fada, har Siyama ta kalleshi. “Gashi” Ataa ta fada tana dauko shi daga gefen Nana ta maida saman jikinta. Har ya bude ba ki kamar ya sake cewa wani abu sai kuma yai shiru ya maida dubansa gurin Nana. “Ya mai jiki” Siyama ta tambaya. “Alhamdulillah da sauki” Ta fada tana kallon Aliyu da fuskarsa ke daure. Juyawa yai ya fice daga dakin ba tare da ya sake cewa komai ba. Siyama tai saurin binta tana ma Ataa Allah kyauta. Rai a bace ya shiga motar yana ta mamakin yadda maza suke sakewa da mace da sun ga kyau su yi ta rawar jiki. “Mtssssssss” Yaja tsakin daya saka Siyama kallonsa kadan tai saurin kawar da kai, tana tunanin abunda tai ba daidai ba da har ya saka shi tsaki. Be shiga cikin gidan ba ya tsaya bakin gate ba tare da ya danna horn ba, Siyama na ganin hakan ta san baya son shiga ciki ne, sai ta bude motar ta fita shi kuma yai ribas ya juya, yana driving wayarsa tai ringing kallonta kawai yai ya dauke kai rabon da yaji ringing din waya indai ta shi ce har ya manta, dan shi baya son ringing sai dai ya bar waya a silent ko vibration. A bakin gate din gidansu Rahma ya faka motarsa sai a sannan ya kai hannu ya dauki wayar yana duba yadda Nasir da wata bakuwar number suka jera masa missing calls hudu ya saka wayar vibration sannan ya shiga text ya aikawa Rahma sako. RAHMA POV. “Kin ga ko Rahma ki daina damun kanki da lamarin namiji, namijin ma wanda zai iya mantawa da ke a take, domin yana jin zai iya zuwa ya dauko wata macen ke ya barki a nan” Cewar Muneera tana wani yatsina fuska. Ikram ta girgiza mata kai. “Wallahi karki dauki zugar Muneera Rahma, Aliyu yana son ki kuma yana kaunar domin ba ko wane namiji ne zai yarda ya auri mace mai ciwo irinki ba har ya nema miki lafiya, yanzu shekara takwas kuna kokarin shiga ta tara amman be taba nuna gazawarsa akai ba, sai ma nuna miki kauna da yake, Wallahi da wata ce ke kamata ma yai ki ce masa ya auro wata ku zauna tare domin shi babban tukuncin mace a gurin mijinta” Muneera ta taba hannu tana dariya. “Lallai Ikram ba ki da hankali, ke baki ganin yadda ya fara gajiya da ita? Wallahi da yana kaunar ba babu abunda zai saka ya ce ba za a cire kodar mai son siyarwa a dasa mata ba, kuma duk inda kodar ta kai sai nemota ya saka mata” “Wacce ta kone yanzu waya saka mata ita ba shi ba, wai ya kike haka ne Muneera zawarcin nan fa ba dadi ne da shi ba, kin kuma sani dan gashi nan kina yi, akan me za ki rika zugata ta kashe auren ta bar mai son tsakani da Allah ta dawo tana nadama” “Wallahi babu nadamar da zata yi, ko sakinta yai alheri ne dan zata iya auren wani ta haihu ta barshi shi da baya haihuwar yana rabon ido, ke ce dai baki san duniya ba tunda ba ki taba auren ba shiyasa kike wannan maganar, anyi karatu amman kamar wacce ba tai ba, ni wallahi na riga na san right dina namiji be isa ya juyani yadda yake so ba” Muneera ce ke wannan maganar tana harar Ikram. Duk abunda suke Rahma bata ce koma, sai dai ta kasa daina hawayen da take saboda kishin da yake damunta. “A tsakankanin kwanakin nan ina jin kamar na rabu da Aliyu, ko dan na samu haihu kuma na matsar da jikina daga nasa, dan ba zan yarda ya hana jiki da wata yar talakawa kuma ya hada da ni ba, amman sai na ji kamar ba zan iya ba, Saboda ina son Aliyu sosai ya saba min da wasu dabi'unsa da ko bachi bana jindadin yinsa ida yadda baya kusa da ni” Tana rufe bakinta sako na shigowa yarta da number Aliyu Sweet bae kamar yadda tai saving number sa da dan emoji din heart a karshe. Sai da ta share hawayenta sannan ta bude sakon ta soma karantawa. _Fito gani gurin gate muje gida_ _Na fi son zama a nan_ Ta mayar masa da amsa a take ya sake aiko mata da wani sakon. _Na sani, a sokoto za mu zauna amman a gidanmu_ _Ka bar ni a nan kawai_ _Ba ke son kulawata ne Rahma? Ba kya son zama kusa da ni ne?_ _Ina so Aliyu ina so_ Ta mayar masa da amsa tana hawaye sai ya sake turo mata wani sakon. _Then fito muje gidanmu I'm waiting for you_ “Wai yana bakin gate” Ta fada tana kallon kanen nata Muneera tai karaf ta ce. “Mi ya zo yi?” “Wai na fito mu koma gida” “Tashi kije, ki fadawa Daddy kawai da Momy sai ki bishi ku koma can idan ma kina son zaman a nan da safe sai ya rika kawo ki” “Ta je fa kika ce tab hmmm” Ikram ta kalli Muneera da tai maganar ta ce. “Karki zuga ta akan abunda kika san gaskiyarsa, namijin da baya fushi idan yai be iya ba, duk yadda yake son ta idan tana masa irin haka zata nisanta sonta ne kawai a zuciyarsa” Saukar da kafafunta Rahma tai daga saman gadon tunawa da Aliyu baya son jira duk kuwa da tasan ita yana daga mata kafa, sai dai idan yai fushi da ita itace zata shiga damuwa. “Bari na fadawa Daddy da Mommyn sai na tafe” “Wai da gaske tafiya za ki yi? Allah mai iko, ni kan kada Allah ya dora min son namiji haka” Kallonta kawai Rahma tai ta ce “Ba za ki gane ba ne, Ikram hada min magani na a jaka” Ta dauki mayafinta ta dora a kafata ta fice daga dakin. ALIYU POV. Yana zaune cikin motar yana ta kallon wayarsa ko zata sake turo masa sako amman shiru, bata turo masa ba kuma baya son shiga ciki saboda iyayenta domin ya lura yanzu kamar basa son auren su. Sai dai yana daga musu kafa kuma yana dagawa Rahma kafa a duk abunda take saboda ya dauketa abokiyar rayuwa, a ganinsa idan mace bata jidadin a gidan aurenta ba to a ina zata je ta  jidadin? And ya san mata karamar kwakwalwa ne da su shi tunaninsa da nata ba daya ba, shiyasa baya biye mata, idan kuma aka zo maganar mata yana raga mata sosai kuma yana daukarta da muhimmanci yana mata uzuri saboda ya san darajar ace wannan matarka ce, duk wani rashin kulawarsa da wulakanta mutane a waje ne ban da matarsa.   Yana hakimce cikin motar Rahma ta bude gate ta fito tana takawa a hankali ta doso inda motarsa take, fita yai daga motar ya bude mata front seat tun kan ta karaso. Hugging dinta ya fara yi kamin ya sumbaci goshinta. “Ya jikinki?” “Da sauki” Ya karbi jakarta hannunta ya saka a motar sannan ta shiga ya rufe kofar ya zagaya ya koma mazaunin direba ya hau titi. MUHSEEN POV. He wake up early saboda jirgin da zai bi na safe ne wanda zai tashi da misalin tara na safe. Gashi kuma akwai aikin da yake son yi a nan kamin ya wuce sokoto. Daga dawoalwarsa Dag masallacin da yai sallah asuba ya nufo part din Mama Fulani dan hadawa kansa ruwan Lipton, yana ta kallon Garejin da Ataa take yana murmushi ya san da tana nan da yanzu ta fito ta shiga aiki, bata wani dade sosai a gidan ba amman na saba da ita kamar wacce suka taso tare, zuwan nan ma saboda ganinta ne yasa yake son yaje saboda yayi missing dinta sosai. Be yi zaton zai samu Mama Fulani a kitchen ba, domin ba halinta ba ne fito tun asuba tai aiki. “Mama ke ce a kitchen yanzu ni na dauka ma wata yar aikin aka samu” Ya fada da mamaki karara a fuskarsa. Ita da murmushi ta kalleshi tana sanye da kayan bachi kana ganin fuskarta kasan tana cikin farinciki sosai. “Ina dai a sake dauko mana wata yar aikin amman tsohuwa na ke so ba yarinya ba” Dariya Muhseen yai ya nufi butar ruwan zafi ya dauko ya zuba mata ruwa yana fadin. “Saboda mi?” “Ai ka fi kowa sani” “Wai tafiya za ki yi ne hala? Naga kina farinciki kuma kin shigo kitchen tun da safe” “Aa Wallahi Abbah ku ne ya fada min jiya da dare bayan ya dawo aiki, kasan maganar kamfanin nan da ake son siyarwa” “Eh wani abun ne” “Wani abokin kasuwanci Abbah da ke can Agadaz ya ji, ya fadawa Babansa sai suka kira Abbah ku suka ce masa suna son za su iya kamfanin su sabunta shi a cigaba da yin komai a karkashin mahaifinku, shima yace shekaranjiya ya samu labarin kamar wasa sai jiya da rana aka jira da number Nijar sarkin ya fada masa jikansa zai zo ya kara duba kamfanin kuma su tattauna akan maganar yau” “Wow amman am so happy for Abbah Wallahi” “For us dai ai wannan dukan mu ne, domin ance mutumen ba shi da keta, sarkin Agadaz ne komai yaransa da jikoki yake wakiltawa su yi shi yana can sai idan wani abun babba ya taso yake zuwa” “Au sarki ne ma amman wannan ya tara da yawa” “Kai ance yana da dukiya sosai, shi da iyalansa, ance duk inda zai je da jirginsa ma yake yawo” “Amman Mama irin wannan anya ma zai ci abincin kin san sun fi son abinci waje fa irin na turawa” “Abbah kune ya ce a shirya masa dan yafi son abincin gargajiya, ai ba sarkin ne zai zo ba jikansa ne, da misalin goma za su iso shiyasa na soma aikin tun yanzu kamin su Maryam su farka su taya ni” “Okay ni kuma da 9 zan je sokoto” “Gurin me?” “Ba na fada miki Aliyu ya kira ni ba akan rashin lafiyar matar nan mahaifiyar Ataa” “Wai a ina ya ganta?” “Oho ai tunda kince a sokoto take kuma yana can ga Momy ma a can nemanta ba zai musu wahala ba” “Muhseen ku fita daga safgar yarinyar nan dan girman Allah, wai kamar ku za a ce kun tsaya kuna bata lokacinku akan wata kazamar yarinya yar matsiyata irin wannan? Haba dai idan ma kyauta ne yake dibarku ai sai ka koma gida Yola ka zabo kyawawan mata suna nan da yawa yayan manyan mutane amman ya yar talaka ba, dan akasan ba zan bari ka auri yar da ubanta baya iya amsa sunansa a garinsu” Murmushi yai. “Mama kenan, yanzu idan wata kaddara ta faru aka ce sai na auri Ataa yaya kenan?” “Babu ma abunda zai faru, kuma ko ya faru ba zaka aureta ba, kai ni fa na tsani yarinyar nan ko sunanta bana son ji” “Gashi kuma naga kamar dan ki sonta yake” “Ai Aliyu ba irinka ba ne Wallahi, Aliyu ya fi karfin yar talaka yar talakan ma wacce tai aiki a gidansu, kawai dai yana kokarin ganin sun rabu lafiya ne kar su bata masa suna kasan talaka da sheri ga hassada” Wannan karon dariya Muhseen yai domin shi a tashi fahimtar Aliyu ya fara son Ataa tun da har zai iya daga waya ya kira shi dan ayi ma mahaifiyarta aiki, mutumen da you can die in front of him ya wuce ya bar ma. Mama Fulani ta aje wukar hannunta ta fito daga kitchen ta nufi dakinsu Maryam. Wutar dakin ta fara kunnawa sannan ta shiga tashinta. “Maryam ku tashi mana ku rika min aiki mu yi mu gama ku yi wanka ko shirya” “Fita za mu yi?” Maryam ta tambaya tana murza idonta. “Ba ko dai za mu yi, kuma idan Allah ya min yadda na ke so ya kamu da son daya daga cikinku” Ta fada tana fita daga dakin zuwa dakin Rukaiyah domin tashinta. ATAA POV. Sam bana jin dadin ganina Aliyu a yanzu, saboda jin kai da yake fama da shi ga uban nuna isa da yake yi kamar shi ya fi kowa a duniyar nan. Wato shi ba zai iya cewa ya jikin Nana ba, ba kuma zai iya shigowa da sallama ba, sai amsawa mutane magana tsaitsaye da gadara. Abincin daya kawo ma kin ci nai saboda shi ya riko dan haka ni ba zan ma ci abincin daya kawo ba. Sai kawai na zuba na rana da Momy ta kawo mana na sake cinsa sannan nai sallah isha'i na kwanta. Ba laifi yau na tashi raina da dan sakewa saboda Nana ta gane ni kuma ta samu bachi mai kyau da allura da Doc nan yai mata jiya domin har yanzu bata farka ba. Duk kuwa da zuciya ta bata aminta da shi sosai ba saboda gudun abunda ya faru ya sake faruwa, sai idan na tuna abunda Allah ua kaddarawa bawa babu mahani sai na kwantar da hankali domin ko dauke Nana nai ban san inda zan kaita ba daga nan, ba ni da kudin magani kuma ban san wanda zai taimaka mana ba, idan ban yarda da Aliyu ba ina kokarin yarda da Momy saboda yanayin da na gani a fuskarta kamar ba zata iya cutar da wani ba.   Misalin takwas da wasu yan mituna Husna da Amina suka shigo suka kawo mana abun karyawa, ina cikin amsa ya mai jikin da suka min Nana ta farka wani abun mamaki sai ta tashi zaune da kanta sai dai fuskarta ta dan kumbura kadan, a nan suka shiga gaisheta suna mata ya jiki ta amsa musu da hausar ta da bata fitowa sosai, sannan suka min sallama suka tafi ba laifi sukan suna da son mutane babu nuna kyama ba kamar su Maryam da Rukaiya ba. Toilet na shiga na dauko karamin bokiti da ruwa a kofi na kawo na wanke ma Nana baki da kaina sannan na zuba tea din da Momy ta aiko mana na bata ta sha sannan na rika ta sauko daga kan gadon ta shiga bandakin da taimakona tai alwala muka fito ina rike da ita na saka mata hijabina tai sallah daga zaune. Bayan ta gama ta koma saman gadon ta kwanta, wani likita ne ya shigo ya dubata ba wacan na jiya mai far'a da son mutane ba, wannan fukarsa a daure take, tsabanin wacan daya sake min fuska ya tambayi sunana da garinmu har ya dauko laptop dinsa ya nuna min rawar yan garinmu. Bayan fitar Doc din wata nurse ta shigo ta bata magani sannan ta fita sai a lokacin ni kuma na zuba abincin ina ci ina amsawa Nana tambayar da take min wai yaushe na dawo. “Tun shekaranjiya, amman baki sani ba” “Bana iya gane komai, na sha wahala sosai bayan tafiyarki Ataa babu mai kula da ni ga yunwa tun ina iya tashi har kai bana iyawa idan na tashi sai na fadi, na yi ta cewa Farida ta kira Maman Salma ta fada miki cewar ki dawo ki kula da ni kamin na mutu amman bata kira ba” Da yaren buzanci take fada min wannan maganar, ban san lokacin da idona ya cika da hawaye ba na aje abincin da nake ci ina kallonta na ce. “Ai yanzu ba zan sake tafiya na barki ba Nana” “Bana son ki sake tafiya ki bar a nan, da ki je neman kudin maganina ki bar ni mutu a wulakance kara ki tsaya kusa da ni a haka na mutu a suturce, kar ki bari na zama ta farko a tsatson sarautar mu da za tai mutuwar wulakanci” “Allah ya raba mu da mutuwar wulakanci Nana ba zan sake barinki ba In-Sha-Allah” Na fada ina share mata hawayenta, sannan na zauna kusa da ita ina dauko mata labarin Abuja sai dai ban yarda na fada mata zancen korata kai ba, cewa nai dawowa nai na ban tsaya na karbi kudin aikina ba domin da sunan ganin gida na zo. “Ki bar musu kudin can ba zaki koma ba, waya kawo ni asibiti?” “Wata Hajiya ce ta taimaka mana” Haka ta fada min ni kuma nai murmushi ina tuna Kamal ko ina yake a yanzu oho. Misalin sha biyu Muhseen ya shigo dakin da muke fuskarsa da murmushi kamar yadda ya saba, ina ganinsa dadi ya lullube ni na hau murna domin na san shi ne likitan da zai mata aikin kuma na san shi ba mugu ba ne kamar Doc Asim ko da yake ba a fuska abun yake ba. “Pretty Pretty” Ya fada yana min dariya sai nima nai masa murmushi. “Sannu da zuwa” “Yauwa ya jikin Mamanmu?” “Da sauki” Ya karasa kusa da ita ya rika hannunta ya sumbace shi sannan yai mata sannu. “Sannu Mamana Allah ya baki lafiya” “Amin na gode” Sannan ya nufi files din da suke nan yana dubawa sai ya fita da su, bayan wani lokaci ya sake lokowa ya kira ni, sai na tashi na fita na same shi tsaye jikin kofar. “Pretty ya kin yi missing dina?” Na yi kasa da kaina shi kuma sai kallon kirjina yake da fuskata kasancewar babu Hijab a jiki. “Wani abun nake son na tambaye ki, miyasa kika bari Mahaifiyarki ta siyar da kodarta?” A take fuska ta canja. “Ba siyar tai ba, likitan nan ne ya cuce mu ya cire mata” “To gaskiya ya cutar da ku, domin aikin nan da za a mata akwai yiyuwar bayan aikin ta iya manta wani bangare na rayuwarta ko ma gaba daya zuwa wani lokaci saboda abun ya taba kwalkwalwarta” “Wani abun zai sake samunta kuma?” Na tambaya hankali a tashe. “No zata samu lafiya amman akwai yiyiwar hakan ya faru shiyasa na fada miki haka tun yanzu, gaskiya likitan nan da Aliyu sun cutar da ku, ko da yake Aliyu ya ce siya yai amman gaya zaka siye abu kamar wannan koda fa guda ace baka mai shi ba kuma har ka yarda kai amfani da ita” Hawaye ne ya fara sauko min sai ya miko min wata takardar da pen ya ce na saka hannu. “Ki kwantar da hankalinki wannan na dan lokaci ne amman zata samu lafiya, saka mim hannu zan mata tiyata” “Muhseen na baka amanar mahaifiyata dan Allah karka cutar da ita” Na fada bayan an saka hannun a inda ya nuna min na mika masa. Sai ya kai dayan hannunsa ya shafa kaina tare da yanjo tsoron dake bayana ya dawo da shi gaba. “Ba zan mata komai ba, ba kowa ne kamar Aliyu ba, bari naje na saka kayan theater amman ki min alkawari ba za ki yi kuka ba?” Na gyada kai ina hawaye. “Good girl” Ya fada sannan ya wuce ni kuma na resina a gurin ina kuka. Wasu nurses ne suka zo da kujera suka dora Nana akai suka fito da ita daga dakin ni kuma nai saurin share hawayena gudun kar na sakata a damuwa. #Team Muhseen #Team Aliyu #Kamal #Team Rahma #Ataa Wane Team ya fi yawa?.🤔 Ni dai Ina Team Rahma kishi gaskiya ne 🙄😏 *ZAKI By Khadeeja Candy 31... Kiran sallah asuba ne ya farkar da shi daga bachinsa da yake, kasancewar karar loudspeaker masallacin ta shigo sosai har cikin dakinsu saboda daukewar wutar nepa da akai misalin uku da rabi na dare. Sake maida idon yai ya lumshe ya saka hannuna na dama ya murza saman fatar idon sannan ya sake budewa ya kalli Rahma dake kwance kirjinsa tana sharar bachinta a hankali. Dagata ya fara yi daga jikinsa sannan na sauko da kafafunsa kasa ya zauna bakin gadon ya dafe kansa ya farka da Ataa a ransa kamar yadda mafarkinsa ma ita ce a ciki, ajiyar zuciya ya sauke sau biyu sannan ya unkura ya tashi jikinsa ba tufafi ya shiga bandaki, wanka ya fara yi kamin alwala sannan ya dauro tawul ya fito ya nufi wardrobe ya dauko karamin jean ya saka ya dora Jallabiya a sama sannan ya dauko kasa ya nufi masallaci. Bayan ya sauke farilla da addu'o'i ya dawo gida yana tafe a hanya yana tasbihi da hannunsa har ya iso, yana kokarin hawa stairs mai gadinsa ya kunna sola gidan ya gaske gaba daya, dakinsa ya shiga ya zauna bakin gadon tare da kai hannunsa yana tashin Rahma a hankali.“Dear tashi ki yi sallah” Daker ta motsa saboda bachin dake cikin idonta domin jiya bata samu bachi da wuri ba daga ita har Aliyu da nuna mata yadda yai maramarinta a tsakanin kwanakin nan. Sai ya tabbarar ta farka sannan ya dauki qur'anensa ya sauko downstairs ya zauna a saman kujera ya bude yana karantawa. Yayi one hour ya a karatun sannan ya hau ya maida qur'anen a nan ya samu Rahma ta koma bachi sanye da Hijab din da tai sallah, Bedsheet yaja ya lulluba mata saman jiki sannan ya sauko ya shiga kitchen, daman idan suna sokoto shi yake shi ke hada musu breakfast ba kamar Abuja ba da mai aiki yake musu. Ruwan Lipton ya fara dorawa sannan ya fasa kwai ya ya kada ya je ya firaye dankalin ya zuba mai ya soma soyawa, da kansa ya share kitchen din bayan gama komai ya zuba a abun zuba shara sannan ya dauko kayan ya kawo dinning. Ya kunna tv ya zauna a gurin yana kallon news baya son ya tashi Rahma a yanzu domin yasan bata saba farkawa da 9 ba sai 10 balle yanzu da yasan ciwon nata yafi na da yafi son ta huta iya hutawa har bachi ya gintse ta.   Yana zaune a falon har 11 Rahma bata farka ba, tana can tana bachin dadi shi kuma yana zaune yana labartawa Nasir abunda ya faru a waya.“Aliyu idan ka nuna Muhseen damuwarka idan yai maka abu, domin idan ya lura kana jin haushi zai yi ta jindadi ne yana ta bata maka rai wanda hakan zai kara bata zumuncinku ne kawai” “Muhseen kanena ne Nasir idan be min biyaya ba kar ya sammaci samun damata da har zai raina ni” “Muhseen kanenka ne, amman babu wanda zai san da hakan sai idan ka fada domin babu wanda zai kalleshi ya ce kanenka ne, kai kuma kana son nuna masa kai ne sama da shi, yes haka ne amman ba ko da yaushe babba yake zama yace dole sai shi a bi shi, wani lokacin kai ua kamata ace ka bi dan a zauna lafiya” “O ni zan bi Muhseen din? Nasir kamar baka san da Aliyu kake magana ba?” “Na sani ma, naga ba kullum take jumma'a ba” “Amman kullum rana ce” Aliyu na fadar hakan ya aje wayar a hannun cushion ya tashi ya hau sama domin duba Rahma, a zaune ya same ta saman gado tana danna wayarta dayan hannunta na saman kanta tana tsifar gashinta. Kusa da ita ya zauna ya sumbace kumatunta. “Good morning ya jikinki?” “Da sauki” Ta fada ba tare da ta kalleshi ba. “Baki sha maganinki na safe ba, bana son tashinki saboda na san kin gaji sosai” Ya fada yana janye hannunta daga saman kanta. “Ki daina tsifar nan karki gajiyar da kanki idan mun ci abinci zan kai ki saloon a gyara miki kai” Sauka tai daga kan gadon. “Bana son fita ko'ina yau na fadawa Mommy ta aiko da mai mata kitso ta zo ta min” Bandaki ta nufa ta barshi a gurin zaune. Bayan ta gama abunda zata yi ta fito sannan shi ma ya shiga ya wanke bakinsa ya fito sai ya same ta gaban madubi zaune tana kallon kanta hawaye na sauko mata. “Wani abun ne kuma?”Juyowa tai ta kalleshi. “Yanzu Aliyu idan na mutu ba zaka wuce wata daya ba zaka mantani ko?” Kallonta yake ba tare da yace mata komai ba. “Idan na tuna ba saboda ni ka zo garin nan ba sai na ji kamar na hadiye zuciya na mutu, ban taba kawowa a raina cewar zaka taba son wata mace ba, watan ma kazama yar aikin gidanka kuma yar bara a titi” “Taso muje mu ci abinci” Shine abunda ya fada yana juyawa. “Ba ka son ayi maganarta ko? Saboda ta fini kyau ta karbu a zuciyarka, saboda kana sonta wata kila ma ka kosa na mutu ka aureta....!” “Rahma....!” Ya kira sunanta a tsawace da duka muryarsa, ba ita kadai ba har kujear da take zaune a kai sai ta girgiza. “control your tongue, Bana son nanata magana kin sani, kuma bana son bata miki rai amman kina kokarin ganin sai na bata miki rai, kin riga kin karya yarinyar kin kuma juya mata baya dan haka babu ruwanki a cikin wannan maganar, idan wani abun ne a tsakanina da ita ne ba da ke ba, lamarinta ya daina damunki kina damuna, ki bar ni na ji da ciwonki da kuma kuskuren da na aikata” Tunda ya soma maganar hawaye yake sauko mata har ya gama ya juya ya fice daga dakin cikin bacin rai. Maganganun da yai mata suna ta maimaita kansu a cikin kunnenta, zata ita rantsuwa ta sake ra tsewa babu kaffara, cewar Aliyu be taba daka mata tsawa kamar haka ba, ko fada sukai ko suka samu tsabani sai dai ya kyaleta ya ki yi mata magana ya daina kulata amman ba fada kamar haka ba. “A a ba zaka auri wata ba Aliyu ko bana da rai balle ina raye, ba zaka so wata ba” Ya fada tana girgiza kai sai kuma ta saka hannunta ta watse duk abunda yake kan miron ta dauki stool din ta jefi ruwan mirror da shi a take ya watse ya fadi kasa tana ihu kamar wata mahaukaciya. Kuka tai sosai har sai da kanta ya soma ciwo kamar ance mata da gaske Aliyu son Ataa yake kuma aurenta zai yi, sai da idonta yai ja sosai sannan Aliyu ya shigo dakin ya daga daga kwancen da take ya rumgume matarsa tsantsan jikinsa.Wani lokacin yana dagawa Rahma kafa saboda ciwonta yasan abu kadan zai iya sanadin tashin ciwonta ko kuma ya saka ta cikin wani hali, idan ma ta yi kishi ai saboda shi tai kuma saboda tana son sa, sai dai hakan ba zai saka ya biye mata ba ta yarda cewar ita kadai zata zauna a gidansa ko a zuciyarsa duk kuwa da ba shi da muradin auren mace sama da daya. Kara fashewa tai da kuka tana jimkeshi da hannayenta. Sun dauki lokaci a haka kamin ya dagota ba tare da ya ce mata komai ba ya saketa ya shiga bandaki yai wanka tana zaune a gurim har ya fito ya shirya a gabanta ya saka agogon hannunsa da atm dinsa da wallet sannan ya kalleta. “Ta so muje ki karya” Kamar mai jira sai ta mike tsaye ta sauri ta bi bayansa domin shi tuni yayi gaba, kamar masu rigengen saukowa daga stairs din haka suka sauko, ita tana sauri ta cin masa su sauko tare shi kuma yana ta lafiya abunsa ba tare daya jira ta ba. Ya riga isa dinning sai yaja mata kujera ta zauna sannan ya shiga zuba mata abincin bayan ya gama shi ma ya zauna kusa da ita ya zauna yana ta lasa wayarsa kamar be san da zamanta a gurin ba. “Ba zaka ci abincin ba?” “Na ci” Ya fada ba tare daya kalleta ba, ba dan kuma ya ci abincin ba. Sai da ta ci ta koshi sannan ya tashi ya koma sama sai ta bishi a ciki ko da ta shiga ta samu yana hada maganinta gurin daya, sannan ya shiga bathroom ya debo mata ruwan tab ya mika mata maganin ta karba ta sha. Sai ya sumbaci goshinta kamar yadda ya saba mata. “Zan fita amman ba zan dade ba zan dawo yanzu” Da kallo ta bishi har ya fice daga dakin sannan ta sauke ajiyar zuciya tana jin tashi motarsa ta dauki wayarta ta kira mahaifiyarta tana kuka.ALIYU POV. Ko da isa gidan Momy biyu ta kusa domin rana ta bude sosai wani gurin ma har an fara kiran sallah. Amina ce da Momy zaune a falon Amina na kwance Momy kuma na zaune suna cin apple. Daga kwance da Amina take ta mikawa Aliyu gaisuwa sai ya watsa mata harara. “Ni za ki gaisar a kwance” Saurin tashi tai zaune ta sake gaisheki sai kuma ya ji amsa mata ya kalli Momy yana mika mata gaisuwa. “Kai komai na ka na zafi ne, shi gasar da mutun a kwance kuma laifi ne?” “Yayanta ne ni fa Momy wannan ai rashin da a ne, je ki duba min abinci” Ya karasa yana kallon Amina, da sauri ta tashi ta nufi dinning. Momy ta sake kallonsa ta ce. “Ka je da safe ka duba mahaifiyar Ataa?” “A a ba mu dade da tashi daga bachi ba” “Kai da wa?” “Rahma” “Au iyayenta sun yarda sun baka ita? Ta dawo?” “Daman ai ba hana min sukai ba, zuwan da sukai a nan ma da ban amince ba da ba zan barta ta zo ba” “Amman dai kasan ya kamata ka je da safe ka gaisa da mahaifiyar yarinyar nan” “Momy ban san rana yayi haka sosai ba yanzu zan je” “Kara ka fara zuwa inyaso idan ka dawo sai ka ci abinci, Muhseen ya zo kuma ban san halin da ake ciki ba, ni bana son zuwa yanzu ina jiran Ramatu ne ta zo muje tare dan na fada mata cewar Daddynku yana da patient a asibiti ta zo ta rika kwanar mana da ita, ka ga ita ma Ataa sai ta samu tana dan hutawa kar dawainiyar tai mata yawa” “Ramatu mai aikin Hajiya Baraka?” “Eh kasan tana da kirki sosai, bana son dauko wani daga gidan dangina ne ko na Daddynku bana son maganar tai ta yawo ne, amman ka ga Hajiya Baraka aminiyatace ba kowa zata fadawa ba” “Muhseen ya zo kik ce Momy?” Ya tambaya yana kallon Amina wacce ta doso inda yake rike da plate din abinci. “Eh nan ya fara sauko kamin ya wuce asibitin” “Ina abincin da za a kai mata?” “Gashi can a dinning” Ya mikawa Amina keys dinsa hannunsa. “Saka min abincin a mota”Hannu biyu ta saka ta karbi keys din ba dan tsoronsa na sai dan Momy ta koya musu haka karbar abu da hannu biyu tun suna kanana domin yana karawa mutum kima da daraja a idon mutane. “Da ya so mi yace? ” “Be ce komai ba, kawai dai yace ya dauka Ataa na nan” Momy na fadin hakan Aliyu ya mike tsaye ya fice daga falon ba tare daya taba abincin ba. Cikin motar ya zauna har Amina ta gama saka masa abincin sannan ya yi ma motar key tun kamin ya danna horn mai gadin ya bude masa gate ya dauki hanyar Usmanu Danfodiyo University teaching hospital wato uduth a takaice. Tafiyar da zata dauke shi minti ashirin da biyar ko ashirin yai ta a cikin minti goma sha sha hudu, a gurin da aka tana dan aje motoci ya aje motarsa ya fito da abincin dake cikin kulolin da kwadon da aka zuba plates da spoon a ciki ya aje a gurin sannan ya rufe motar. Tunanin yadda zai dauke su yake dan baya jin zai iya maya biyu yaje ya dawo dan daukar abinci kawai. Wata budurwa ya kalla ta sha kwaliyar kanti tana tsaye jikin wata farar mota sai yauki take kamar miyar kubewa da alama wasu take jira. “Ke zo nan” Ya fada kai tsaye kamar wacce ta sani ko kuma daya daga cikin kanensa yana kallonta fuskarsa babu alamun wasa. Kallonsa budurwar tai daga sama zuwa kasa farar shadda ce a jikinsa ta yi mugun karbarsa kamar wani ango fuskarsa nata haske ga farinsa sai shining yake, ta kuma lura da makekeyar expensive car din da dake yake tsaye kusa da ita ta san tashi shi domin alamun naira sun nuna a jikinsa. Ta nuna kanta tana wani lauye baki kamar wata karuwa.“Ni....” Be ce mata komai ba sai kallonta yake, ita bata jira yace ita din ko ba ita ba sai ta karaso kusa da shi tana wani rangwada kamar zata karye. “Dauki kulolin nan ki biyo ni” “Okay” Ta fada yadda take pronouncing o din is like tana koyawa mutane karatu ne. Shi ya rika kwandon yai gaba ita kuma ta riko kulolin karama da babba ta bi bayansa zuciyarta na raya mata cewar ya kyasa da ita. Kai tsaye suka wuce ciki tana biye da shi har suka shiga dakin da mahaifiyar Ataa take. Inda taga ya aje kwandon ta karaso ta aje kulolin tana kallon Ataa wacce ke zaune saman gadon hawaye shar a fuskarta a zatonta ita ce bata da lafiyar. “Sannu ya cikin” Ta fada tana wani lankwasa harshe kamar wata bakanuwa. Hannu Aliyu ya saka aljihu ya ciro wallet dinsa ya zaro dubu uku har zai dora a saman gadon asibitin ya ce ta dauka sai kuma ganin Ataa yasa ya mika mata da hannunsa. “Aa ka barsu kawai” “Karba mana bana maida kudi” Hannu ya kai ta karba. “Thank you” Ta furta tana juyawa ta koma tana ta sauraren ta ji Aliyu ya kirata ko ya biyo bayanta amman bata ji ba har ta fice. Ko be tambaya ba yasan an shiga tiyata ne da Mahaifiyar Ataa tunda Momy ta fada masa Muhseen ya zo kuma gashi be tarar da ita cikin dakin ba. Kallon Ataa dake zaune kan hospital bed din Aliyu yai with serious face ya ce. “Mi akai miki kike kuka?” Bata ce masa komai ba bayan turon karamin bakinta da tai ta saka hannayenta ta share hawayen fuskarta. Wata kila tsoron tiyatar da aka shiga da mahaifiyarta take ko kuma wani abun akai mata, or maybe Muhseen ya fada mata wata maganar ne marar dadi.“Ga abinci” Dauke kai tai. “Bana ci” A tunaninsa ko tana tsoron kar ya saka mata wani abun ne ko kuma ya cutar da ita shiyasa ba zata ce. Kujerar da ke gefen gadon ya janyo ya zauna ya dauki plate din ya zuba jalop din da sannan ya bude dayar kular ya zuba farfesun kazar da ke cikin ya saka spoon ya soma ci, abinci yake ci amman idonsa akan Ataa ne har ya ci rabi ya mika mata sauran. “Karbi ki ci” “Na ce bana ci” “Idan na ce ayi abu yi ake ba a musa min karbi ki ci na ce” Kallonsa tai hawaye na mata zuba. “Ai babu wanda ya isa ya cilasata kai yi Aliyu, sai dai ka cilasta wasu, babu wanda ya isa ya taba wani naka balle ya taba ka, yadda kaga dama haka kake haka kake juya kowa, ka taka kowa ka cilasta ka zalinci wanda ka ga dama saboda kana da kudi ni kuma kana gani na talaka” “Ba ni na cirewa mahaifiyarki koda ba, lokacin da aka cire mata koda ina a gurin ne kin gan ni ne?” Ya fada yana kokarin danna fushinsa. Sai ta girgiza kai “Baka nan, amman kudinka suna nan, ikonka yana nan, isarka tana nan waya sani ko asibitin taka ce? Kai ma baka son talaka miyasa ka sakawa matarka kodar talaka? Karyar soyayya kake mata tunda baka iya daukar kodarka ka saka mata ba, ba tana da iyaye ba miyasa basu bata kodar su ba? Sai ta Nana matar da ita kadai ta rage min a duniya? Kokarin kare kanka kawai kake yi ai Muhseen ya fada taya za a sakawa matarka kodar da baka san mai ita ba? Duk wannan taimakon kana min ne saboda ka san ka zalince ni ka cutar da ni ni da mahaifiyata Aliyu kai azzalumi ne....” Cikin wani irin fushi marar misatuwa ya jefar da plate din hannunsa ya mike tsaye yana huci kamar zai dake ta, sai kuma yai saurin kawarda fuskarsa daga barin kallon yana kokarin saita numfashinsa. Mikewa tai tsaye wanda hakan yai daidai da shigowar Doc Bukar dakin, tana kallonsa fuskarta da hawaye ta ce. “Na fada Aliyu ka kashe ni daman mutuwa ta fi rayuwa a yanzu, ka riga ka gama da ni tun da kasa aka cire mahaifiya koda dan zalinci ka sadawa ita ta rayu mu sai mu mutu, ga mahaifiyata can ana mata aiki Muhseen ya fada min zata iya mantawa da komai ciki har da ni har da ni Aliyu, idan kuma bata rayuwa ni ce a cikin matsala saboda zalincin da kuka mana kai da wannan likitan, har abada ba zan yafe muku ba kuma Allah ba zai bar ku ba....” Ta fada kanta a sama tana kallonsa hawaye ke mata zuba sosai har wani dauke numfashi take kamar zata shude... Jawur idon Aliyu sukai yana kallon Ataa take rabe masa uku ba ko biyu babu ko kyafta ido. Doc Bukar ne ya matsa kusa da su yana Kallon Aliyu sai kuma ya kalli Ataa. “Zauna” Ya fada sannan ya kalli Aliyu. “Da za ka fita na wani lokaci” Sai a lokacin Aliyu ya kalli Doc Bukar ya sake kallon Ataa sai kuma ya nufi kofa ya fice cikin wani irin bacin rai marar misaltuwa.Ba zai iya fadar lokaci da ya kawo gurin motarsa ba wata kila ma taku biyu yai ko uku ko kuma dari ko dubu shi dai kawai ya samu kansa tsaye jikin motarsa ba tare da ya san ya iso ba saboda tsananin bacin rai da zafin kalaman Ataa, wani irin gudu jinin zuciyarsa ke yana da tabbacin da za a bude kirjinsa a yanzu wata kila da hayaki za a gani yana tashi. Ita kadai ta kai haka duk duniyar nan ta fada masa magana irin wannan mai zafi da daci kuma ya kyaleta ita kadai ce mutum ta farko da ta taba taba martabarsa da duk wani abun daya takama da shi tana a talakarta ta fada masa magana son ranta. Bude motarsa yai ya shiga ciki ya zauna for like 40 minutes sannan yai mata keys ya fita daga harabar gurin. Driving kawai yake ba dan yasan inda zai je ba, gida gurin Rahma ko kuwa gurin Momy? Ko gurin wasu abokansa ko yan'uwa? Kalamanta na ta maimaita kansu a kwakwalwarsa tun yana jin zai iya jurewa har ya kai ga runtse ido yana damke sitiyarin motar, sam ya manta cewar tuki yake kuma babban titi yake na gawon nama, har sai da yaji ya bugi wata motar wata motar kuma ta bugu bayan tasa, da sauri ya bude ido yana kiran mafi kyawun sunan a cikin sunayen Ubangiji wato Ya Rahamanin Rahim. Saurin tsayarda motar yai motar da ke gabansa tai gaba shi kuma ya faka tashi gefe ya fito ya nufi mai motar. “Malam lafiya kake kuwa?” Mutumen ya tambaya. “I'm sorry ina cikin matsala ne” Aliyu ya fada sannan ya bude wallet dinsa ya ciro sababbin kudi da zasu kai 50k ya mikawa mutumen. “Ga wannan” Mutumen ya kalli kudin kamar ya karba sai kuma ya dan tsaya jan aji. “Ai ba kudi ba... ” “Idan zaka karba ka karba kawai ba zan tsaya magana da kai ba na fada maka ina da matsala” Hannun mutumen ya kai ya karbi kudin yana dan nuna kamar be so ba. Aliyu ya juyo ya bude motarsa ya shiga mutane sai kallonsa suke yai mata key ya sake hawa titin yana ta tasbihi saboda samun fin karfin fushinsa. Wani guri ya samu can kusa da ga ďan k'ane hotel ya faka motarsa ya fito yana shakar iskar gurin. Har yanzu ya kasa daina jin kalaman Ataa a kunensa sai dai wannan karon a maimaikon ransa ya bace kamar dazun sai tausayinta ya soma rabar zuciyarsa fiye da da, yarinyar da ke tsoronsa da masu kudi tun da har ta iya bude baki ta fada masa magana irin wannan tabbas tana cikin damuwa da bakinciki, ya sani ko Ataa zata fahimcin ba nan kusa ba kuma ba a yanzu ba. Yanzu ma laifin ba nata bane na Muhseen ne, for what zai fada mata cewar mahaifiyarta zata manta da ita? For what zai mata karyar cewar da hadin kan Aliyu aka cire mata koda? Komawa yai cikin motar a fusace ya dauki hanyar gidansu Momy. **ZAKI By Khadeeja Candy 32... Abinci kusan kala hudu Mama Fulani ta shirya ma bakon da zaizo, ko da tara tai gaba dayansu sun shirya Maryam da Rukaiya sukai wanka Baby ce kawai ta wuce scul. Amman shiru bako be iso har goma da rabi. Sai misalin sha daya Abbah ya kira yace mata bakon ya sauko Nigeria gashi nan ma zai taro shi a airport. A sannan ne Mama Fulani ta saka su maryam suka kwashi kulolin abincin suka jera part din Abbah, ita kuma ta kunn turaren wuta irin mai kamshin nan sosai na larabawa ta kara kunna dayan ac sannan ya dawo part dinta, a daki ta samu su Maryam da Rukaiya sai kara gyara fuskarsu suke suna fesa turare. Wani dadi ne ya lullube ta ganin duka yayan nata sun fito fes gwanin sha'awa. Suna jin tsayawar mota sukai hanzari yafa gyalensu suka jiyo bayan Mama Fulani dake cikin wata shadda yar mali ta sha paint work gwanin sha'awa.   Mota biyu ce ta Abbah da kuma wata mai tsada da suka shigo, ta kamfaninsu da ke nan Abuja. Suna fitowa daga motar Mama Fulani na fitowa ita da su Maryam suna musu marhabun bakin Mama Fulani har kunne, a maimakon mutum daya sai suka ga samari biyu dayan sanye da kananan kaya dayan kuma sanye da farar shadda ya nada bakin rawani a kansa kamar wani balarabe. “Lale marhabun Lale lale marhabun da manyan baki” Mama Fulani ta fada tana kokarin sauka daga balcony din ta nufi inda suke, sai duk suka saki murmushi suna kallonta. “Sannu da zuwa” Maryam ta fada kamin Rukaiyah ta dora da nata. Dayan ne ya amsa yayinda yadan kuma yake ta kallonsu yana murmushi kamar baya jin abunda suke fada. Abbah ne yai gaba zuwa part dinsa yana musu iso sai suka bishi a baya, bayan sun shiga ciki sun huta ne Abbah ya shigo part din Mama Fulani ya kira dan taje su gaisa da su, sannan ya shiga bangaren Ammy ya same ta falonta zaune ita da yaranta suna kallon wani film da ake hassaka a mbc Bollywood.Ganin Abbah yasa Batula da Zainab tashi zaune suna murna domin ba su san da shigowarsa ba sai ganinsa a falon. “Sannu da zuwa” Ammy ta fada tana dariya, sai ya zauna kusa da ita yana kallonta. “Yauwa Hajiyar gida, ban fada miki za'ayi ba ki ba?” “Na sani na fada min, amman naga ai Hajiya Fulani ce zata shirya komai ko?” “Ko dai zata shirya ai ya kamata ku gyara ku fito ku tarbesu, na fa sha fada miki cewar bana son yawan kebe kanki da kike yi” “Bana son yawa shiga Safgar Hajiya Fulani ne, bana son nai mata abunda zai zo ya zame mana matsala ko ka zo kana mim fada” Be sake ce mata komai ba ya kalli yaransa. “Batula ku tashi kuje ku gaisa da baki” Gaba dayansu suka tashi suka Batula ta tashi ta shiga dakinta ta dauko mayafi Zainab kan haka ta fita ita Humaira daman abaya ce a jikinta da dankwali, Abbah ya biyo bayansu yana jerowa da Ammy Inteesar kuma na rike da hannunsa suka nufi part din. Ko da suka shiga Mama Fulani na zaune saman kujera tana watsar hakora Rukaiya da Maryam kuma na zaune a kujera daya ko wacce na duba wayar hannunta ala ala kowa waccensu take daya daga cikinsu ya ce yana sonta. Ganin Abbah tare da Ammy ya mugun batawa Mama Fulani rai, domin ita kwata kwata bata son yana kula Ammy da yayanta, sai dai kawai ya ji da ita da yayanta. Abbah ya zauna yana nunawa bakin nasa iyalansa sannan ya juyo yana fadawa Mama Fulani. “Wannan Sunansa Amir saboda yana da sunan Mai Martaba da shi shiyasa ake ce masa Amir baya jin hausa sai faransanci da buzanci sai kuma English wanda shi gama duniya ne a yanzu, wannan kuma Sunansa Usman shi yana jin hausar” Da turansanci Maryam ta shiga gaishe da Amir din da idonsa ke kan Zainab, ya amsa mata ita da Batula sai ya sake kallon Zainab wannan karon sai da suka hada ido. Da yaren faransanci Zainab ta gaishe shi sai ya amsa mata yana dariya tare da tambayarta wai ashe tana jin faransanci, sai tai dariya ta soma fada masa cewar ta yi karatu ne faransa ita da Batula, bakinciki kamar ya kashe Mama Fulani domin shi ma dayan ta lura Humaira yake kallo yana ta murmushi gashi ba ma wata kwaliya sukai kamar na yayanta ba.Bayan sun gama gaisawa ne sun fice Abbah ya kira wani daga kamfanin ya zo suka soma nuna masu yadda abubuwan suke, ba dan ba su sani ba sa dan kara tabbatar musu da komai a agabansu. Daga bisani suka fito domin zuwa ganin cikin Kamfanin, a lokacin ne Ammy da yaranta ita da Mama Fulani suka fito gaba dayansu suna musu sallama domin daga can ba za su koma ba zasu dawo nan ba. Usman ne ya ciro kudi mai yawa ua bawa Inteesar ya ce su raba, sannan ya ciro wasu ya bawa Ammy da Mama Fulani, Amir kan sai da ya shiga mota a side din da yasan Abbah ya ba zai hango su ya sauke gilashin motar yacs ta Zainab ta zagoyo cikin yaren faransanci sannan ya rufee glass din. Zagayowa tai kamar yadda ya bukata sai ya mata sallama sannan ya mika mata katinsa da kudi mai yawa wai su raba. Godiya tai masa sannan ta matsa baya dayan ya shiga mota Abbah yaje ya shiga tashi suka bar gidan. “Kawo kudin nan?” Mama Fulani ta fada rai a bace sam bata jidadin yadda ya kira Zainab ba. “Batula karbi ki bata” Ta fada tana mikawa Batula kudin kamin Batul ta karba suka fadi kasa bata tsaya komai ba ta juya zata tafi sai da Ammy ta daka mata tsawa. “Zainab dawo ki dauki kudin nan ki bata” Juyo tai ya dawo ta duka har kasa ta dauko su ta karaso gurin Mama Fulani ta mika mata. Wani bakin haushi Mama Fulani ta ji ganin kati a hannunn Zainab tasan bata shi yai. “Wato rashin kunya za ki min ko? To bari ubanki ya dawo sai wani kadadi take jikinta na rawa wai ita ta ga maza” Uffan Zainab bata ce mata ba, saboda Ammy na tsaye a gurin kuma ko ba komai tasan Mama Fulani matar mahaifinta ce be dace tai mata rashin kunya ba. Fisgar kudin Mama Fulani tai har kumbarta na yagar hannunn Zainab. “Fitsararriyar yarinya marar tarbiya” “Zainab tana da tarbiya Hajiya Fulani domin uba daya ya tarbiyantar da su” Cewar Ammy cike da jin zafin yadda Mama Fulani take ma yarta tana jan hannun Inteesar su nufi part dinta, daman tuni Mama Fulani ta karbe kudin hannun Inteesar. “To ai daman na san ke kike koya musu yadda za su min rashin kunya da rashin kamun kai an ga maza sai karkadi ake ba ko kunya” Mama Fulani ta fada cikin daga sauti tana bin bayan Ammy da yayanta da harara. Kamin su juya su koma ciki Maryam uwar masifa bakinciki ya hana ta cewa komai domin ita kan ta kyasa da ganin Amir din.Sai da suka zauna a falo sannan Mama Fulani ta kallesu. “Ku kuma kun wani cika hoda kamar aljanu ai dole ba za su ga yadda ainahin kyauku yake ba” “Ba wani rashin ganin kyau wannan kwaliyar da ke maida mummuna mai kyau ma, kawai dai bakij asirin Ammy ne ba banza take ba rinsu ba, tun da dai ba kyau suka fi mu ba” Cewar Maryam tana wani bata fuska tana cin magani. Rukaiya ta tsire baki. “Haka fa ranar muka fita da Inteesar wani ya zo yana ta daukar mata kaya sai rawar kai yake, ga ni ni babban amman Wallahi ta Inteesar kawai yake har da wani cewa Antynmu za ki ba ni wannan? Sai da na ce masa Abbah mu fada yake idan yaga ma muna magana da maza sannan ya kama kansa” “Waya sani ko asiri tai muku ma? Ni fa abun nan har mamaki yake ba ni da tsoro ga kunan Masha-Allah da ku amman ace babu wanda zai zo ya taya, idan an zo ba za a koma ba, sai wani jikon ke Maryam Kamal din nan ke kawai yake zuwa gurinki shima sai can ba a rasa ba yanzu kuma yana ganin wannan shegiyar yarinyar Ataa ya koma kanta har ta kai mu ga tsabani” Maryam ta kalli Mama Fulani da ke zancen ta ce. “Nima fa abun yana bani mamaki Wallahi, kin ga zata iya mana mu aki mu ita a so yayanta, ba ki ganin yadda Abbah yake rawar jiki da ita?” “Ai ku ba ku san komai ba, ni nan na san komai lokacin da aka kawota tana amarya a gidan nan sai kun ga yadda Abbah ku yake rawar kai da ita, ina tunanin tun can gidansu aka shirya mata ko minene sai da na tashi tsaye sannan na samu yancina a gidan nan, amman barta ko yanzu ai ba zan zura muku ido ba, shekara nawa da kare makaranta kunan babu mai shinshini, amman ita ko jiya na ga Batula tana tadi da wani” Mama Fulani na fadin haka Maryam ta tashi ta nufi upstairs cikin wani irin haushi abunda ya faru.ATAA POV. Zaunawa nai kamar yadda Doc Bukar ya bukata shi kuma ya fice daga dakin. Fita Doc Bukar yai a dakin be dade ba ya dawo dauke da gorar ruwa da tissue ya miko min, karba nai na share magina da hawayena sannan ya bude gorar ya dauki kofi ya zuba ruwan mai sanyi ya ba ni, da na sha sai na ji wani sanyi a raina har an samu sauke ajiyar zuciya. “A karo?” Na girgiza masa kai alamar a a sai ya karbi kofin ya aje ya zauna a kujerar da Aliyu ya tashi yana kallona. “Za mu iya magana?” Na kalleshi tare da gyada masa kai ima ta shisshikar kuka. “Siyarda kodar mahaifiyarki kika yi wa Aliyu ko?” “A a cirewa yai da karfi shi da wani likita, cin amanata yai ya zalince ni” “Kamar ya ba da saninki ba?” A nan na labarta masa abunda ya faru tun daga kan saran macijin har kawowa yanzu. Tausayina ne ya bayyana a fuskarsa karara wayarsa na ringing ya ki ya daga sai kallon yadda na ke hawaye yake. “Na san Doc Asim kwararen likita ne mai zaman kansa, kuma likita da zai iya komai saboda kudi, wata kila ya yaudare ki ne ya cire kodar ya siyar musu” “Taya mutum zai siye koda be san mai ita ba? Taya?” Na tambaya cikin kuka, sai dan risino kusa da ni yana kallona. “Ba lallai ne sai Aliyu ya san da hakan ba, kuma ina tunanin idan Aliyu ya sani ba zai karyata ya ce miki be sani ba, domin na san Aliyu tun ba mu san kanmu ba, he's my childhood friend mun dade a tare, da ya sani zai amsa miki ya sani ko da kashe shi za'ayi, Aliyu mutum ne kai fi daya, idan yace maka yes go yes din ne ko dai ka yarda ko karka yarda” “Wata kila ya yi hakan ne dan ya kare kansa” “Idan kokarin kare kansa yake, kotu zai kai ki yace zaki bata masa suna, ko ka ya saka a koreku daga garin nan, domin Mahaifin Aliyu babban mutun ne mai mutunci a garin nan ko a gurin gobna yake so abu a take ake masa, ko dan saboda gudun bacin suna zai iya sakawa a koreku ko kuma ya kyaleki mahaifiyarki ta mutu ke kuma ki shiga wata rayuwar kin ga shikenan ko? Amman har jininsa ya bawa mahaifiyarki jiya gora uku aka saka mata, zan iya yarda Aliyu yayi kuskure na rashin bincikar inda kodar ta fito, kuma zan iya runtse miki cewar ba da hadin bakinsa akai miki haka ba, kudin aikin da akai ma mahaifiyarki ma a yanzu shi ya biya kuma ya biya na magani da komai and ya fada min cewar yana son mahaifiyarki a raye”Sai yai kamar be ji me nace ba ya nufi gurin jinin yana gyarawa sannan ya ce. “Ba zata farka da wuri ba wata kila sai nan da awa 48, ba lallai ne idan ta manta komai ya zama ta tuna ba, ba lallai ne kwakwalwarta ta dawo ba” Kasa ce masa komai nai domin na fahimce na kuma fahimci abunda yake fada. “Gaskiya kin yi kuskuren barin mahaifiyarki tana cikin wannan ciwon na tsawo lokaci haka, da an dauki mataki da yanzu duk hakan ba zai faru ba” Har yanzu hawaye kawai nake har bana iya ganin fuskar Nana da nake kallo. Ko da na yarda cewar Aliyu ba da saninsa aka min haka ba, ba zan taba iya ganin kimarsa ba har abada, domin saboda matarsa akai wa Nana haka. Ji nai an dago fuskata sai hawayen suka kwanto min na ga fuskarkar Muhseen da ke kallo na ido cikin ido. “Mahaifiyarki zata tashi ta ji sauki na tabbatar miki wannan, amman ba zata iya gane wacece ke ba ba kuma zata iya tuna komai ba, sai dai karki nuna mata cewar akwai wata rayuwa ta baya da tai a yanzu, sai nan da wani lokaci idan ta fara shan magani” Sai a lokacin na iya bude bakina na amsa masa da to ina kawar da fuskata daga rikon da yai min. “Kar abunda Aliyu yai ya dame ki, ke dai ki maida hankalinki gurin neman lafiyar mahaifiyarki kawai kina mata addu'a” “To” Na fada murya can ciki, sai na zauna a kujerar da ke nan na rumtse idona ina hawaye. Ina jin lokacin da ya fice daga dakin ya bar nan a nan na samu damar yin kukana na tausayawa kaina kuma na tausayawa Nana na halin rayuwar da muke cikin, ban taba tunanin za mu jidadi ba amman a kullum ina fatar zata samu sauki mu cigaba da rayuwar mu kamar yadda muka saba. Misalin biyar da rabi Momy ta zo ita da wata bakuwar fuska ta riko mana lemu da ayaba da kankana. Na gaishe ta da muryata mai sautin kuka sai ta amsa min tana kallon yanayi na. “Ataa ki kwantar da hankalinki Mahaifiyarki zata samu lafiya ta tashi In-Sha-Allah” “Muhseen ya ce idan ta farka zata manta da komai, ba zata iya tuna komai ba kuma ba lallai ne tunaninta ya iya dawowa ba” “Innalillahi wa'inna ilaihirraji'u, kuma dai? Kai Subhanallahi wannan abun babu dadi ji” Ta fada cike da tausayawa sannan dakin yai tsif kamar babu kowa a ciki. Ni ina hawaye ita kuma tana ta kallona ta kasa yin komai.Shiru nai ina nazari maganarsa, wata kila da gaske be sani wata kila kuma shi ma wannan likita hadin baki yai da shi kamar wacan dan ya wake kansa. “Idan na akan kuskure yai ko kuma da ganganci na bar shi da Allah shi da duk wanda ya cuce ni Allah zai saka min” “Allah zai kwatar miki hakki ki a nan duniya ko kuma gobe kiyama, na jidadin da kika san da hakan kuma kika yarda, Aliyu kuma be biya ni ko ya roki na fahimtar da ke haka ba, hasalima bansan cewa da zalinci aka cire miki kodar ba sai yanzu, sai dai na san da zalintar yai da ba ki isa ki tsaya a gabansa ki fada masa magana mai daci haka ba, idan har shi azzalumi ne a take zai batar da ke ua shafe labarinki a doron kasa, dan haka ki kwantar da hankali ki daina damun kanki da wata damuwar a shekarunki” Hannu nasa na share hawayena na kawar da fuskata. “Na sani uwa tana da muhimmanci dole ne za ki ga abunda akai miki da fadi, amman ki rika tsayawa kina tunani a ko wane lokaci kamin ki aikata abu” Mikewa yai tsaye ya fice ba tare da ya sake ce min komai ba. Ni kuma na kwanta a saman gadon ina jin zuciyata tana min wani mugun zafi, idan har Nana ta manta da komai ciki har da ni ban san yadda zan yi rayuwa ba, addu'a kawai nake ina rokon Allah kada ya kaddara hakan ta faru. Sai kusan la'asar aka fito da Nana daga dakin tiyata, ko da aka dawo da ita dakin tana bachi suka saka mata jini tare da lullube ta da zanen da Momy ta aiko mana. Ni kuma na tsaya a kanta ina ta kallonta hawaye na ta min zuba kamar ba gobe, tsoro nake kar abunda Muhseen ya fada ya zama gaskiya. “Ke wai ba ki gajiya da kuka ne?” Muhseen ya fada bayan ya shigo dakin yana nufo inda nake tsaye ina kallon Nana. “Anyi tiyata cikin nasara sai dai fatar samun sauki, dan haka ki daina kuka” Dagowa nai na kalleshi. “Yanzu da ta farka mantawa za tai da ni ko?”Daga tsayen da take ta zo kusa da ni ta tsaya ta kai hannu ta dafa kafadata. “Wata jarrabawar da sauri take zuwa wata da dadewa wata kuma sai daga karshe, wadanda take zuwama daga karshe sun fi shan wahalar rayuwa, amman daga ta zowa a lokacin kurciyarsu sun fi kowa jindadin rayuwa a gaba, ina jin tausayinki sosai ba ba dan saboda jinina ne silar hakan ba, sai dan halin da kika tsinci kanki tun kamin rayuwar ta kawo ki nan, labarinki abun a tausaya miki ne a tallafa miki, tun daga lokacin da ya fada min abunda ya faru ban taba ganinki ba amman sai na samu kaina da tausayinki, daga lokacin da na saka ki a idona kuma sai na fara miki kallon yata, ba fata na ke ba amman ko mahaifiyarki bata raye ni nan mai rikonki ce kuma na kula da ke, ki kwantar da hankalinki Ataa In-Sha-Allah za ki samu duk wani jindadi da wata rayuwar da kika rasa a baya” Fashewa nai da kuka kalaman da take min sai nake jin kamar Nana mutuwa zatai ta barni, idan ko ta mutu na shiga uku bana da kowa sai Allah. Sai shida har da yan mintuna sannan Momy ta tashi zata wuce gidan. “Wannan matar sunanta Laraba zata rika kula da Mahaifiyarki ke kuma kina dan samu kina hutawa, kamar yanzu za mu iya barinta sai ki bini muje gida idan kina so, kin ga sai ki samu ki yi wanka ki huta kamin ta farka” “Aa ni dai ki barni a nan, na fi son ko zata farka ta farka a gabana, ji nake kamar idan nai nisa za ta mutu ta barni” “Ba zan takura ki ba, amman ita ma zata zauna a nan tana da waya a hannunta kinji kina bukatar wani abu ki yi mata magana zata kira ta fada min” “Tau” Na fada ina kallonta da idona da suka gama kumbura. Kudi ta ciro mai dan dama ta mikawa matar wacce ta kira da laraba. “Ki rike wannan idan tana bukatar wani abun sai a siya, kuma kin san halin yarinya sai dan lallaba duk da nasan ba halinki bane fada amman dai a kara, bama son abunda ya taba yarinyar nan yanzu” “To Hajiya In-Sha-Allah za a kiyaye” Daga haka tai min Allah ya kawo sauki ta fice ta bar ni da matar mai sa'ar Nana.Bayan na gama sallah magariba na dawo saman kujerar na zauna ina ta kallon Nana zuciyata na min wani irin zafi, babu abunda ya dame ni a yanzu kamar sanin dangina, lallau rashin yan'uwa a kusa da mu ya saka mu cikin rayuwa mai wahala da tsanani. A yanzu kuma da nake da bukatar sani sai a ace min zata manta da komai? Kife kaina nai a gurin nai ta kukana har aka kira sallah isha'i, sannan na shiga bandakin nai alwala na fito na shimfida carpet na gabatar da sallah isha'i ita kuma tana zaune a saman tabarma tana waya. Bayan na gama sallah na kwanta a gurin ina da hawayen da a yanzu suka zame min kamar farilla. Har ta gama wayar ta tashi tai nata Sallah ta bude abincin dazun ta zuba min a plate ta aje a gabana. “Ki ci abinci” Sai da tai maganar na tuna cewar ban ci wani abinci na bayan na safe. “Bana jin yunwa” Na fada ina kawar da kai daga barin kallon abincin da warinsa ma baya min dadi. Jan plate din tai a gabanta ta soma ci, ni dai ina a gurin har dare ya soma yi. Jin nai zaman dakin ya ishe ni ina marmarin wani gurin dabam ba nan ba, fita nai daga dakin ba tare da na fada mata ga inda za ni ba ita ma bata tambaye ni ina zanje ba. Fitowa nai harabar asibitin ina ta kallon yadda fitilun asibiti da sukai haske har suna kashe min ido domin idon nawa sun yi laushi sun kuma rage haske saboda kuka da nake. Mikewa nai ya fito daga cikin asibitin ba dan nasan inda zanje ba. Wani bangare nake tunawa na rayuwarmu daga zaman da muka saba yi a bukka da kuma baran da muke har zuwa rasuwar Lukman. A da mu biyu ne yanzu kuma na zama ni kadai, ina tuna lokacin da Baba yake da fada cewar wata rana zan maza a yarta wata kila yana da rai ko kuma bayan ransa, har ya kama hannun Lukman yana wasa ya ce. “Ban so rayuwar mu a haka ba, ban so komai ya zama yadda yake yanzu ba, amman wata rana komai zai zama tahiri, Lukman sai zama babban mutum Ataa kuma ki zamu gata mai kyau, sai dai ban sani ba ko kusa ne ko kuma nesa, idan ina da rai zan jidadi idan kuma bana da rai sai ku min addu'a kun ji” A lokacin da yai wanann maganar yana rike da hannuna da na Lukman. Yawun bakina na hade ina magana da kaina. “Baba ka rasu, Lukman ma ya tafi, tsakanin ni da Nana ban san wanda zai riga wani ba, amman ina fatar na rigata, sai dai wannan jindadi da ka ce mana ba zai zo ba har a bada”Hawaye ne ya sauko min a haka na kamo hanyar Clapperto ina hawayen har na iso, cikin dakin kwanon na shiga na kwanta daga bakin kofa ina kallon taurarin dake sama hawaye na ta min zuba na kasa tsayar da su. ALIYU POV. Be iya labartawa Momy abunda ya faru ba, domin yasan ita ma ba fahimta za tai ba, wata kila ma shi zata dorawa laifi sabanin Muhseen. Yanayinsa kawai ta gani tasan yana cikin bacinrai, Momy tana ganewa idan Aliyu yana cikin damuwa da bacinrai. Karya yai mata dan kar ta tambaye shi ya ce mata kansa ke ciwo. A gidan ya wuni har yamma sallama masallacin unguwar yai. Bayan la'asar Momy ta shirya ita da Laraba wacce ta iso suka kama hanyar Asibitin, Momy na fita Husna da Siyama suka tashi suke shige daki gudun kar su yi wani abun yace am masa ba daidai ba, daman Amina tun da ya shigo gidan ta tare a daki tana kallonta. Bayan fitar Momy da mintuna kadan motar Muhseen ta shigo cikin gidan, a kusa da motar Aliyu ya fakata ya fito ya nufo kofar falon. Knocked ya fara yi kamin ya tura kofar falon ya shiga. Aliyu na zauna saman cushion yana kallon Muhseen har ya karaso cikin falon, be ce da Aliyu komai ba ya nufi kitchen a zatonsa Momy na can. “Kana aiki kamar baka san aikin ka ba Muhseen, taya zaka fadawa karamar yarinya kai tsaye cewar mahaifiyarta za manta da komai?” Muhseen ya juyo ya kalleshi. “Wani likitan ne zai fada min idan na yi kuskure amman ba mai kula da Sky Global Resources ba, aikin kamfani kake Aliyu baka san komai akan aikina ba” “Yes aikin kamfani nake, shiyasa na iya sarrafa halshe na san irin maganar da zan fadawa kowa, ba kamar kai ba da zaka tashi hankali yarinya karama kana fada mata maganar da bata kamata ba” “Miyasa tashin hankalinka zai tashi hankakinka Aliyu? Saboda kar cutar da kai mata ta fito fili ko kuma saboda akwai abunda kake boye?” Aliyu ya masa banza yana ciro wayarsa ya danna. “Son ta kake yi ko Aliyu?” “Son ta nake yi ko akwai abunda zaka yi? Yanzu ma kaje ka fada mata cewar ina son ta shikenan” “Very funny” Muhseen ya fada yana dariya sannan ya nufi kitchen din. Aliyu ya bishi da wani kallon banza. “Zan yi kokarin hana duk wani kusanci na ku ko kebawa ka fada mata magana son ranka, ba zan kyaleka ka rika shigar mata jiki ba kana son cutar da zuciyarta da ita sakare kawai” Shine abunda Aliyu ya fada a ransa sannan ya tashi ya fice daga gidan gaba daya zuwa gidansa.Be samu Rahma a idan ba, hakan kuma be bashi mamaki ba domin ya saba mata da fita ba tare da ta nemi izininsa ba. Sai dai a tsakanin yau da ta fita da kuma wacan zuwan daga Abuja zuwa nan ya bata masa rai matuka. Yana zaune a gidan har magariba babu abunda yake tunani sai Ataa, ta masa maganganu masu zafi amman yai mata uzuri saboda tana cikin damuwa da bacin rai, zancen zata manta kowa ya fi komai tsaya masa a rai shi yana mamakin yadda ciwon kodarta zai taba kanta har ta manta da kowa. “All this saboda ni oh Ya rabbi ashe haka jarrabawar nan take? Ni kuma tawa kenan?” Ya furta yana tsaye jikin karfen stairs yana sauraren kiran sallah isha'i da ake. Komawa yai ciki yai alwala ya fito ya shiga masallacin unguwar yai sallah daya dawo be ma shiga falon ba ya shiga motarsa zuwa gidan Momy. Ko da ya shiga Momy ta shirya abincin dare na su Ataa tuwo da miya. “Ga abincin ta nan ka je ka kai mata” Ko zama be yi ma Momy tai masa wannan maganar. Kai tsaye ya nufi dinning ya dauki miyar Siyama ta saka masa tuwo da plates Momy tana ce masa idan ya kai ya dauko na can a wanke. Tare da Siyama ya tafi asibitin saboda ta rika masa kulolin, bayan yayi fakin ya fito tana gaba yana baya har suka shiga ciki. Wannan karon ma be shi sallama ba sai dai Siyama ta fanshe shi tun da ita ta yi sallamar. Bayan sun gaisa da Laraba yai ta rabon ido ko zai ga Ataa be ganta ba. “Ina Ataa?” Ya tambaya yana kallon Nana. “Ta fita tun dazun” “Ina taje?” “Bata fada min inda zata je ba” Fitowa yai sai Siyama tai saurin daukar kayan ta biyo bayansa ta saka su a mota ya kama hanyar gida.A bakin gate ya gaje ta ragowar kulolin ma sai da mai gadin ya rika mata ta shiga da su, sai ya koma cikin asibitin. Harabar ya tsaya yana ta kallon mutane kamin ya sake komawa ciki a zaton mai gadin ward din Aliyu likita me dan haka ya bude masa kofa da kansa ya shiga duk kuwa da kasancewar dazun ya ganshi da wata yarinya tana dauke da kuloli. “Bata dawo ba?” Ya tambaya daga shigarsa dakin. “Eh har yanzu” Juyowa yai ya fito ya dawo cikin motar ya zauna yana ta tunanin inda zata je cikin daren nan, wata kila Doc Bukar ya fita da ita ko kuma Muhseen daman be ganshi cikin gidan ba lokacin daya shiga, fargabarsa daya baya son ta kebe da wani gudun faruwar wani domin shi yana ganin ba ko wane namiji ne zai iya kallonta ya kawarda ido ya hade yawunsa ba, musamman ganin bata da kowa. Key yai ma motarsa yana rage ac cikin ya fito daga cikin asibitin ya nufi Clapperto road domin ya duba can, idan kuma har bada can gida zai koma ya saka Momy ta kira Muhseen shi kuma ya kira Doc Bukar. Slowly ya shiga cikin unguwar ya kashe hasken motarsa yana tukawa a hankali har ya isa gidansu Farida. Karasowa yai da motar har dakin kwanon ya matsa ta can inda kofar dakin take ya sauke gilashin motarsa yana hango dakin mai duhu da farin wata ke haskawa, fitowa yai cikin motar a hankali ya nufo dakin ya haska screen din wayarsa daga nisa ya hango Ataa a kwance ta takure guri daya tana bachi kanta na gurin kofa. Wani dogon numfashi yaja ya sauke sannan ya koma cikin motar ya zauna ya bar kofar motar a bude. Idan ya tafi ya barta be san abunda zai iya samunta ba, idan kuma ya tashe ta wata kila wata bakar maganar zata fada masa ko kuma tai masa ihu. Sosai ya so ya tafi sai kuma ya ji ba zai iya kyaleta wani ya zo ya yaga mutuncin ta ba, idan ta kara shiga wani halin a yanzu yana jin kamar shine sanadi, kwantar da kujerar motar yai ya jingina yana ta kallonta tana bachi sai sauke ajiyar zuciya take har shi ma bachin yai gaba da shi. *Khadeeja Candy ce* ZAKI By Khadeeja Candy 33... Ban kwanta da niyar bachi ba na kwanta ne kawai na wani lokaci da zimmar idan na dan hutu tunanin ya fita a raina na koma asibitin, daga nan bachi yai gaba da ni ban sake sanin inda nake ba sai da sanyin azuba ya soma saukowa kiran sallah ya karade ko'ina sannan na bude idona mika nai ina jin yadda jikina yake ciwo saboda kwantarwa da nai a takure ga kuma dadewar da nai a kwancen. Hango mota na facing din inda na ke yasa ni saurin tashi zaune kamin na mike tsaye ina kallon kotar duk da kasancewar akwai hudun asuba sai dai a akwai wutar nepar gidansu Farida da ta hasko inda muke ba kamar Jiya dana kwanta babu nepar ba. Gabana ne ya soma faduwa ina ta tunanin inda babbar mota zata fito irin wannan, sai kuma nake ganin kamar na taba ganin kalarta sai dai ba zan iya shaidar ta waye ba, wani karin abun tsoro kofar motar a bude take kuma babu kowa a ciki. Na hade yawu ya fi sau a kirga saboda tsoro gabana sai faduwa yake. Koma nai can kuryar dakin ina ta kallon ko zan samu wani abu na boya, tsoro duk ya kamani sai a yanzu nake ganin wautata na kwantawa ni kadai a gurin yanzu idan sace ni aka zo yi fa ya zanyi? Idan kuma wani abun za a mim babu mai cetona. Hawaye na fara yi a take na dan tako zuwa gurin kofar ya leko kaina, ina lekowa Aliyu na dago kansa ya kalleni yana zaune a gurin ya jingina da kwanon dakinmu wani abun mamaki a kasa ba tare da ya shimfida komai ba. Saurin komawa nai cikin zuciyata na raya min cewar ba shi ne ba, domin shi mai girman kan tsiya da kankantar da mutane ba zai zauna a nan ba, idan ma ya zauna mi zaiyi? Amman idan ba shi ba ne waye? Aljani? Domin kamaninsa da na wacan Aliyu bil'adam daya ne. Sake kai kaina nai zan leka sai shi ma ya leko cikin dakin. “Ataa kin tashi?” Jin muryarsa yasa na tabbatar da cewar shi din ne, amman kuma me yake yi a nan? “Aliyu ne?” Banza yai min kamar ba zai amsa min ba. “Fito muje gida gurin Momy kamin mutane su taru” Ya fada yana kabe kasar dake wandonsa. “Kai din ne?” Na tambaya dan tabbatar, nan ma be amsa ni ba ya nufi motarsa ya shiga, wannan miskilancin nasa kadai ya isa ya tabbatar min da cewar shi din ne dai ba wani ba.Fitowa nai ba dan na daina jin tsoron ba sai dai wannan karon ba zan iya musa masa ba. Takawa na fara yi ina kallon fuskarsa da wayar hannunsa ke haskawa sakamakon danna ta da yake. Zagayawa nai dayan side din idonsa n kan wayarsa amman hakan be hana shi sanin na karaso kusa da motar ba sai hannunsa ya mika ya bude min motar ni kuma na shiga ina kallonsa har ya janyo murfin motar ya rufe be dauke idonsa daga kan wayar ba. Nima na rufe gefena sai yai motar key ya kunna fitilar motar a sannan ya daga kansa ya kalli gabansa yana ribas kamin ya dawo kan hanya mu fito daga cikin kwanar mu hau titin Clapperto road. Kallonsa nake ina ta mamakin yadda mutum kamar Aliyu mai taka ma da kudi da ji da kai ga isa zai zauna a gurin kamar wannan. “Miyasa ka zauna a nan gurin?” Ya kai minti biyar zuwa bakwai kamin ya amsa ni har na dauka ba zai amsa ni ba. “Idan na barki kika kwana a nan wani abun ya same ni kuma ni za ki dorawa laifin ai, kin fita ba ki fadawa kowa inda za ki ba” Ya fada still be kalleni ba. “Sa gaske kwana kai kana gadina? Da gaske gadina kai?” Sai a lokacin ya kalleni be ce min komai ba ya faka motarsa gaban wani masallaci sai da ba kusa da shi sosai ba ya fita daga cikin motar ya bar wayarsa a nan. Ajiyar zuciya na sauke har yanzu na kasa daina mamaki ina ganin kamar ba gaske ba, maganganun Doc Bukar nata dawo min akai. Ni dai ina zaune a gurin har yai sallah ya fito ya dawo cikin motar, ashe ma daga masallacin zuwa gidan Momy babu nisa sosai domin tafiya kadan yai muka iso bakin gate din gidan.Sau daya ya danna horn sai kuma ya kalli inda na ke har lokacin kallonsa nake kallon mamaki da tunani. “Bana son kallo na sha fada miki” Dauke kaina nai daga barin kallonsa na maida idona gurin yatsun hannuna da nake juyawa cikim dayan hannun, har aka bude gate din jikina be daina ba ni cewar idonsa na kaina ba, mistakenly na dago kaina sai muka ido kallona yake sosai kamar mai son ganin wani abu a fuskata saurin maida kaina nai kasa sai aka bude mana gate din sai a lokacin ya dauke kansa daga gareni ya tuka motar ya shiga ciki, daf da kofar falon ya faka motarsa ban jira ya bani umarni ba na bude na fito kamar yadda na ga ya fito, yana gaba ina binsa a baya a hankali har muka isa gurin kofarz jikina nata kamshin turarensa daya cika motar. Knocked yai sau daya be sake yi ba har na wani lokaci sannan na ga ya dora wayarsa a kunne. “Zo ki bude mana kofar falo” Ko minti biyu be yi da sauke wayar ba Amina ta bude mana kofar falon, a maimaikon ya fara shiga sai ya tsaya kallona da ido ba zai iya cewa na wuce ba sai dai so yake na fara shiga kamin shi. Ina ganin hakan na wuce ciki sannan shi ma ya shigo daya saka wayarsa aljihu. “Shiga da ita ciki tai sallah” Wani kallo Amina tai min kamin ta sake kallon Aliyu tai saurin dauke kai. “Zo muje” Ta fada tana nufar upstairs. Kallonsa nai na ga ni yake kallo sannan na dauke kaina na bi bayan Amina. Dakinta ta kai ni ta nuna min bandaki na shiga na yi alwala ko da na fito har ta shimfida da min carpet da Hijab dina nai sallah sannan na mike tsaye da zimmar fita daga dakin zuwa kasa sai na ji ta ce. “Ya ce wai ki kwanta ki huta”Saman gadon ta na hau kamar yadda ta nuna min na lulluba da bargo mai laushi ya lumshe idona ba dan bachi ba, sai dan tunanin kwanan da Aliyu yai yana gadina wai har yana tsoron kar wani abun ya same ni, abunda wani mutum be taba min ba, babu ruwan kowa da inda zan kwanta ko da ko gurin mai cutarwa ne balle har ayi gadina idan ba mahaifiyarta ba, amman a karon farko wani ya yi gadina kuma yana tsoron wani abun ya same ni, wanin ma Aliyu mutum mai girman kai da ji da kai mai kyamar talaka, idan har na boye na ce ban jidadin abunda yai min hakika na yaudari kaina. Unkurawa nai na sauka daga kan gadon na nufi kofa na fita daga dakin daman Amina ta fita daga dakin tun bayan data fada min sakonsa. Tun da na fara takawa zan sauko downstairs ya dago daga zaune da yake samanb kujera yana kallona har ya sauko. “Ina son naje gurin Nana” “Koma ki kwanta sai idan za a kai abinci za a wuce da ke” Ya fada fuskarsa babu alamar wasa, juyawa nai na dawo dakin na sake haye gadon na kwanta, amman bachi ya ki daukata har rana ta bullo, ba dan komai ba sai dan tunanin abunda Aliyu yai a yau da kuma son ganin Nana da zuciyata ta kwadaitu da shi. Ji nai an turo kofar dakin an shigo hakan yasa na bude kaina daga cikin bargon ina kallon Amina data shigo rike da brush ta mika min. “Ki shiga bathroom din nan akwai man goge baki ki zuba a kai ki wanke bakinki kuma ki yi wanka” Har ta fadi hakan sai kuma ta nufi bathroom din tana fadin. “Bari dai na hada miki ruwan wanka” Bayan wani lokaci ta fito tana rike da brush din a profile zuba mai akai ta mika min. “Idan kin yi wanka ki dauro tawul ki fito karki maida kayan za a kawo miki wasu tufafin” “To na gode”Na fada ina nufar bandakin, wanke bakin na fara yi sannan nai wanka da ruwan data hada min da kuma sabulu mao tsada na dauki tawul din da na gani rataye na daura sai ya tsaya min iya jinyoyina. Haka na fito daga bandakin na samu gafen gado na zauna, bana son na taba wani abu ta zo ta ga na mata ba daidai ba, na fin son sai idan ta zo ta fada min man da zan shafa. Ina zaune ina kallon yatsun kafata masu tsawo kuma sirara na ji an bude kofar dakin na yi zaton Amina ce sai na ga Muhseen yana rike da wayarsa. daga can bakin kofar da yake ya tsaya yana kallona tun daga kaina har zuwa kafafuwana, daman rabin cinyata a waje suke. Ba zan iya fassara mana'anar kallonsa ba, domin a yadda na ke makaskanciya ban yi zaton wani mutum mai daraja dan masu daraja wato nera zai min kallon sha'awa ba, balle har yai tunanin yi min wani abu, sai dai yaba kyauwo na wannan na san wani abu ne da ba ko wane namiji ne zai iya rike bakinsa daga furtawa ba, sai miskilin mutum kamar Aliyu wanda nake ganin kamar ba shi be taba ganin kyau nawa ba domin be taba yaba wa ko nuna zai yaba din ba, kallon ma da yake min ina jin kamar na kurilla ne dan kawai nai magana ko kuma na tsargu. Ya dade yana kallona kamin ya karaso kusa da ni yana ta yawo da idonsa a kan surar jikina. Tsarguwa na soma yi irin tsarguwar nan ta jin haushi idan wani na kallonka tsabanin Aliyu da bana jin haka, ga kuma kallon da yai min lokacin da nake canja tufafi da lokacin da nake wanka, sai na soma jin ba dadi duk kuwa da kasancewar kallon mace ko tana jikinta a gurina ba wani abu bane, domin kuwa da wani babban abu ne da Nana ta zaunar da ni da fada min a matsayinta na mahaifiyata. “Na rantse da Allah kina da matsifar kyau Ataa, look at you karamar yarinya da ke amman Allah ya miki sutura komai ya ji” Ya fada yana kokarin zama kusa da ni sosai yana kallon kirjina da fuskata.Na sani kyau na daga cikin abunda yake burge Muhseen ba tun yau ba tun a lokacin da ya taba ganina a gidansu da sunan aiki ya umarce mahaifiyarsa cewar a zabe ni saboda kyau, sai da yadda yake koda kyau nawa har mamaki yake ba ni domin shi ma yana da na shi kyau daidai gwargwado. “Ataa....” Sunana kawai ya fira be fadi abunda yake da niya ba, sanadin shigowar da Aliyu yai dakin hannunsa rike da mug fuskarsa babu annuri yake kallona da kuma Muhseen. “Wai kai baka jin kunyar kanka? Ka shigo cikin daki ka kebe da yarinya kamar wannan kuma da tawul kawai a jikinta? Ji yadda ka zauna jikinka na kusan taba nata” Muhseen yayi murmushi yana mikewa tsaye. “Ina ce yanzu nan Amina ta fada min cewar kai ka kawo ta, waya san inda ka fito da ita? Kai da ba a zarge ka ba? Kao kullum na zaka kyautatawa mutane za to ba? Ka dinga min abu kamar baka san inda na fito ba? Ko kuma mai mim fatar sheri? To yanzu muka fara tsakanina da kai Aliyu dan kana son ta be isa ya hana ni sonta ba, kai ma din ban san kalar son da kake mata ba” Yana fadar hakan ya fice cikin bacin rai. Aliyu kuma ya nufo inda nake zaune ciki ba fada. “Wai ke baki san haramun ne mutumen da ba muharramin ka ba ya kebe da kai?” “Be min komai ba” “Oh sai ya miki komai ne zai zama matsala? Kallon jikinki ko taba jikinki shi duk ba matsala ba ce? Ba ki tana sani ba?”Na gyada kai alamar ban sani ba din. “Wace makarantar islamiya kika yi?” “Bama zuwa makaranta saboda bara” Na amsa masa ina dan turo baki kamar an min wani abu. Kallona ya rika yi irin kallon nan na mamaki jin furucina. “To haramun kallon jikin mace da ba muharramar ka ba, kin san abunda ake nufi da muharrami ma?” Na sake girgiza kai alamar ban sani ba. “Kina cikin matsala” Na fada yana juyawa sai kuma ya juyo ya ya nuna ni da tsaya. “Kar na sake ganin kin zauna kusa da wani namiji, kar ki sake sakin jikinki har wani namijin ya gani ko da ni ne ko wani can dabam kuma ki kama kanki bana son yadda kike sakewa da kowa” “To” Na fada ina gyara daurin tawul din a kirjina sai ya matsa kusa da ni ya miko min mug din hannunsa. “Ki shanye yanzu za ku tafi asibiti” Hannu biyu na saka na karba garin karbar hannuna ya taba na shi. “Kar hannunki ya sake taba nawa idan za ki karbi abu, kar kuma ya sake taba na kowa” Yana fadar hakan ya juya ya fice daga dakin. Ni dai ban da binsa da kallon babu abunda nai yi. ALIYU POV. A fisace ya fito daga dakin ya rasa dalilin son shiga jikin Ataa da Muhseen ke yi, ya sani Muhseen ba dan iska ba ne amman ba shi da tabbacin zai iya rike kansa be fadawa Ataa ba, shi kansa a yadda ya ganta a yanzu haka ya ji wani abu dabam balle kuma Muhseen da kyau mace kadan kan iya jansa balle kuma Ataa ba zai iya misaltata da kowa ba.A falon ya samu Muhseen zaune yana lasa wayarsa Momy kuma tana kitchen ita da Amina da Siyama hada breakfast. Be cewa Momy ya tafi ba ya fice daga falon zuwa cikin motarsa. Sai da ya dauki hanyar gidansa sannan tunanin abunda zai fadawa Rahma ya fara fado masa a rai, be so yayi bachi a can ba, shi be san ma lokacin da bachin yai gaba da shi ba, and ko da ya farka tsakiyar dare ne gashi ta jera masa miss calls din da be san adadinsu ba, idan har ya daga be san amsar da zai bata ba, idan kuma yace ya dawo cikin dare a wannan lokacin be san irin kallon da zata masa ba, kuma be ji zai iya tafiya ya bar Ataa a nan ta kwana ita kadai, da ya barta a nan ba shi tabbaci shi din zai kwana a cikin natsuwa da kwanciyar hankali kamar yadda ya kasa samun sukuni har sai da ya jingina da kwanon dakin da take kwana, domin yana jin idan ma babu mutun wata kila wani abu mai cutar kamar kwari ko dabba za su iya zuwa su cutar da ita duk kuwa da ya san ba a daji take ba. Driving din yake yana juya kansa dan kwanan da yai cikin motar kamin ya fito juyansa ya yi ciwo ga sanyin dake sauka sai ya saka kansa yai masa nauyi. A harabar gidan yai parking ya fito yana saka wayarsa aljihu ya nufi kofar falon kai taaye ba tare da tsoro ko tunanin komai ba. Kamar yadda ya tsammata a tsaye ya samu Rahma cikin falon fuskarta futik futik alamar ta sha kuka har ya gode Allah. “Ina ka kwana Aliyu?” Ta tambaya tana doso inda yake idonta cike da hawaye. Tsaye yai yana kallonta har ta karaso kusa da shi. “Ni ya kamata na tambaye ki ina kika je saboda ni na aje ki ba ke kika aje ni ba, na zo gidan nan da rana ban same ki ba” “Ka sani kuma kai ka bani dama idan ma na fita ba ya wuce na je gida ko kuma gurin kawaye na, amman kai baka kwana a gida ba Aliyu, kuma na ta kiran wayarka baka daga ba, na kira Siyama ta fada min baka gida ina kaje?”“Fushi nai na bar gidan na kwana a gidan gona na dauka ko ba zaki dawo ba” “Amman baka saba haka ba, kuma baka taba yi ba Aliyu” Ya rika fuskarta da hannayensa biyu yana shafa kumatunta da babban yatsansa. “Karya zan miki?” “Amman.... ” Be bari ta fadi abunda zata fada ba ya hade bakinsa da nata ya shiga aika mata da wani irin sako mai muhimmaci da girma, sakon daya sauko masa tun a lokacin da yai arba da surar Ataa wace rabin jikinta kw waje, cinyoyinta gashin kanta ta ya jike da ruwa ya kwanta a jikinta da goshinta ga fari da kuma gurin wuyanta da ke ta sheki. Tsayuwar ce ta gagaresu har ta kai ga yayi baya ya jingina da kofar falon, sai kuma juyar da ita ta zama ita ce jikin kofar shi kuma ya mata rumfa. Duk yadda Rahma ta zo ya hakura har su isa daki kasa hakura yai daman haka yake idan abun ya bijiro masa baya jira kuma baya iya yiwa mace uzuri matukar uzurin ba na musmmman ba ne, domin Aliyu ba shi da hakuri a wannan babin.A falo sukai komai daga bisani ya rumgume matarsa suka shiga bedroom dinsa a tare sukai wanka kamar yadda ya saba mata bayan sun fito ya saka wasu tufafi ita kuma ta daura tawul domin babu tufafinta a dakinsa, a kan gadonsa suka kwanta yana rumgume da ita har bachi yai gaba da shi. Be farka ba sai da aka kara kiran sallah azahar, shi ya riga sauka saman gadon ya shiga bathroom ya dauko alwala fito sannan ya tashe ta, sai da ya tabbatar ta tashi zaune sannan ya sumbanci goshinta. “Tashi ki yi sallah” “Aliyu motar na ga ya fashe a gaba” “Yeah accident muka samu amman da sauki Allah ya tsare babu abunda ya faru” “Garin ya? Allah ya kare tsarewa” “Amin” Ya fada tare da daukar agogonsa ya daura a hannun sannan ya fice daga dakin yana fadin “Na tafi masallaci” Da kallo ta bishi har ya fice, sannan ta kawarda idonta ta dafe kanta ita dai har yanzu bata gamsu Aliyu ya kwanta gidan gona saboda ta fita ba, be taba haka ba be kuma tana haka ba. MUHSEEN POV. Ransa be taba baci kamar yau ba, ya rasa dalilin daya saka Aliyu yake shigar masa hanci, iyakar abunda ya sani yana son Ataa saboda tana kyau kuma ya san ba haramun bane son mace mai kyau and yes Ataa ta kai mace da za a kalleta a so ta, daman ya dade yana som aure mace mai kyau, bayan son na aure ba shi da wata manufa zuwa ga Ataa amman yadda Aliyu yake masa ya sashi jin haushi sosai,a yanzu ne ya shirya taba ta ko kebewa da ita da kuma neman aurenta domin ya lura kamar Aliyu yana kishi ne, ba taba ta ko kebewa da ita kawai ba ya dauki alwashin har kiss sai ya mata a gaban Aliyu sai dai idan mutuwa zan yi ya mutu idan kuma ya fusata shi sai ya yi mai gaba daya daman dai aurenta zai yi dan haka yana jin ko kaiwa yai a jikinta ba wani abun ba ne face samun damar da zai saka Mama Fulani da duk wani da zai masa karan tsaye ya amince ya aureta. “Muhseen” Momy ta kira shi da karfi jin tana ta kiransa kadan be amsa ba tana can wata duniyar yana tunani. Kallonta yai sai yai murmushi. “Momy magana kike?” “Ina ta magana baka ji ni ba, lafiya dai?” “Wallahi Momy ba lafiya ba, abunda Aliyu yake min ne bana jindadins akan yarinyar nan” Momy ta zauna a kujerar dake kusa da tashi. “Mi yake maka? Daman Husna ta fada min jiya kun yi fada miya faru?” “Momy bana da halin nai magana da yarinyar ko na kebe da ita sai ya saka zargi, kuma wallahi Allah ya sani bana da wani manufa akanta bace na aurenta” Da mamaki Momy ta kalleshi. “Aure kuma?” “Eh na taba fada mata tun a lokacin da take Abuja cewar ina sonta, Mama ma ta san da maganar sai dai bata yarda da ni ba, kin san yadda take tsanar talaka tana ganin kamar kaskancine na auri mace kamat Ataa, amman ni har ga Allah ina son ya Momy dan Allah ki shige min gaba” Ya fada yana wani marairaicewa kamar zai saka kuka.Maganar sam ba tai ma Momy dadi ba sai dai ba zata muna nuna masa ba. “Amman Muhseen yarinyar nan yanzu ba soyayya ko aure ne a gabanta ba, ta mahaifiyarta take” “Na sani Momy, ni ma ban yanzu nake nufi ba, sai hankali ya kwanta, amman Momy ke kadai zan iya rikewa domin ke nake da tabbacin za ki fahimtar da Mama kuma ki share min hawaye na” “In-Sha-Allah ni mai maka komai ne Muhseen, bari na tashi na kira ta fito muje asibitin na gama abincin” Momy ta fada tana mikewa tsaye cikin yanayin na rashin jindadi. *Khadeeja Candy* ZAKI By Khadeeja Candy 34... Bayan fitar Aliyu Amina ta sake shigowa dakin ta dauko min man shafi na shafa sannan ta ba ni tufafi na saka ta fesa min turare da kanta. “Gaskiya kina da kyau Aisha mashallah ga gashi, na ga har kin fi Mamanki kyau ma” Na yi murmushi ina kallon kaina a madubi. “Baba na biyo Babana yana da kyau sosai” “Gaskiya ba laifi kina da kyau sosai Wallahi” Kasa nai fa kaina ni kaina a yanzu sai na ga kamar na fi da kyau, domin jan yadi ne a jikina irin mai fitar da kyau farar mace. “Bari na gyara miki gashinki” Ta warware min gashin kaina ta ta dauko wani katon mataji ta shace min kaina ta saka min jan ribbon daga kasa kuma ta barbarza shi a bayana, sannan ta daura min dankwali ta shafa min kwalli a ido har zata shafa min jan baki sai Momy ta shigo. Murmushi na gani a fuskarka ita kanta da kalleni sai da ta yaba kyau na. “Ai tayi kyau a haka Amina karki shafa mata jan baki sai kace wanda zai je gurin biki, ta so muje asibitin sai ki karya a can” “Tau” Na amsa ina mikewa tsaye sai amina ta dauko wani karamim mayafi ta dora min a kafada. “Dan Allah Momy dan tsaya nai mata hoto” Wayarta ta dauko tai min hoto ta sai kuma ta dauke mu tare sannan na bi bayan Momy daman ta dade da fita daga dakin.Ko da na fito babu kowa a dakin sai Muhseen yana zaune saman kujera yana cin dankali a plate ganina yasa shi mikewa tsaye yana kallona fuskarsa da murmushi. Kofa na nufa sai ya kira ni. “Ataa...” Tsayawa nai na kalleshi ba tare da na amsa ba har ya karaso kusa da ni ya kai hannunsa zai taba fuskata sai na kwace, fadada murmushinsa yai ya saka dayan hannunsa aljihu. “Aliyu ya ce miki wani abu kaina ne? Ya ce miki ni dan iska ne ko?” Na yi kasa da kaina ba tare da na ce masa komai ba. “Ba dan iska ba ne ni, tun na ke a rayuwata ban taba aikata zina ba, dan kuma na ce ina son ki saboda kina da kyau ba laifi ba ne, shi kanshi da ba ki da kyau da ba zai kula ki ba” Ya dan yi shiru kamin ya sake kallona ya ce. “Ina miki fatar alheri ina fatar yanzu ma kije ki samu mahaifiyarki ta farka, kuma ina miki bankwana zan wuce Abuja yau, zan dawo satin sama amman lallai ne idan na dawo yin aikin na biyo ta nan ba, maybe ki ganni nan kusa maybe kuma sai nesa ina mik fatar alheri” Dagowa nai na kalleshi sai ya sakar min murmushi ya nufi kofar fita daga falon ya bar ni tsaye ina juyo na kalleshi. “Aisha” Kiran Momy na yasa na fito daga falon na same ta gurin mota, a front seat na shiga ita kuma ta zauna a mazaunin direba tai ma motar key aka bude mana gate muka kama hanyar asibitin.Ban san dalilin rashin jindadin kalaman Muhseen ba, yanayinsa da yadda yake min maganar ba cikin farinciki ba ne, and i feel like kamar ba zai sake dawowa ba, wata kila wani abun Momy da Aliyu suka ce masa shiyasa ya yanke wannan hukuncin, wata kila kuma ra'ayin kansa ne ban sani ba amman sam kalamansa ba su min dadi ba. Bayan Momy ta yi parking motar ya na bude na fita ita ta bude ta fito sannan ta fito da kayan na rika wasu ta rika wasu muka nufi cikin asibitin, kusan mutane duk wadanda nake cin karo da su babu mai kallo ďaya mazan dai duk wanda ya kalleni sai ya sake kallona wasu har da sakar min murmushi suke. Ni dai in biye da Momy har muka isa cikin dakin da Nana take, Doc Bukar muka samu a ciki da Laraba Doc Bukar na duba Nana wacce ki kwance idonta bude tana kallon mutane, Momy ce ta karasa cikin yayinda ni na tsaya bakin kofa ina kallonta na kasa karasawa tsoro na ke kar na je kusa da ita tace min bata gane ni ba, Doc Bukar na ta sakar min murmushi ni kuma idona na kan Nana har na fara hawaye. “Karaso mana Ataa” Cewar Doc Bukar daker na iya daga kafana na fara takawa cikin dakin, karar sautin takalmin kafata ne yasa Nana ta kalli inda na ke wani abun mamaki sai na ga ta sakar min murmushi, dadi na ji da sauri na karasa kusa da ita ina ta kallonta kamar zan cinye ta. “Nana” “Na'am Ataa” Mantawa nai da tiyata ce a jikinta ya rumgume ta ina kukan dadi, bata manta ni ba ko da ta manta komai ni bata manta ni ba, sai da Momy ta dago ni tana dariya ta ce. “Karki ji mata mana yi a hankali” Na kalli Doc Bukar ina hawayen farinciki na ce. “Doc bata manta ni ba” “Bata manta komai ba sai dai ki yi mata fatan samun lafiya” “Al-hamdulillah Allah mun gode maka” Na fada ina daga hannuna sama, dadin da make ji a yanzu ba zan iya misalta shi ba, duk wanda ya kalleni ya san ina cikin farinciki a wannan lokacin, ba ni da wani buri face samun lafiyar Nana da alama muka yanzu ta doro hanyar samun.Kasa cin abinci safen mai saboda murna sai an nemi yunwa na rasa, Ita kuma Momy ta hada mata tea ta bata da kanta a hankali tana sha har ta sha ya isheta. “Na gode Momy Allah ya saka muku da alheri” Murmushi tai ta aje kofin tana fadin. “Ba komai ai yi wa kaine” Ta dade a asibitin sannan ta fita ita da Laraba wai zata je gida tai wanka ta gyara ta dawo. Aka bar ni asibitin ni da Nana ina kula da ita, cikin muryarta na marasa lafiya take tambayata. “ataa ina kika samo mutanen nan? Suna da kirki sosai” “Wannan matar dan ta ne ya taimaka mana, daga gidan da nai aiki a abuja ya biyo ni zuwa nan na fada masa matsalata da kuma dalilin aikin da nake a can gidansu an Abuja shine ya fadawa Mahaifiyarsa sai suka taimaka mana suka kawo ki asibiti ya biya kudin aikinki kuma jinin da aka saka miki jiya ma ance shi ya bada jinin, kuma yanzu haka a gidansu nake zaune su suka ba ni wannan tufafin ma” “Allah dai yana da kirki sosai Allah ya saka masa da alheri shi da babarsa, bayan Doc Asim mun sake haduwa da wani mutum mai taimako” Na yi shiru ban ce komai ba, domin Doc Asim ko sunansa ba na son a ambata. ALIYU POV. Daga masallacin da yai sallah ya wuce gurin Momy, duka kanensa suna zaune tsakar falon suna cin abinci a plate daya, a tare suke gaishe shi ya amsa musu da dan sakin fuska sai dai ba Sosai ba ya nufi dakin mahaifiyarsa. Zaune ya same ta gaban madubi tana shafa mai a jikinta, juyo tai ta karba masa sallamar da yai tana kallonsa.“Wa'alaikassalam” “Momy barka da rana” “Yauwa, ka je asibitin kuwa?” “No yanzu da na ke son na leka, ban sani ba ko wa a wuce da wani abu shiyasa na biyo” “Yau Ataa tana cikin farinciki” Ya kalli Momy da mamakin farincikin nata, Momy bata jira ya tambaye ta ba ta ce. “Mamanta ta farka kuma bata manta komai ba” “Wow” Ya fada yana murmushi. “Har tea na bata ta sha, yau Ataa har da min godiya” Ya dada fadada murmushinsa shi kansa ya jidadin jin hakan balle kuma da aka ce masa Ataa tana farinciki, ya gyara zamansa yana kallon Momy ya ce. “Ban sani ba ko idan na fada miki wani abu za ki yarda” “Minene?” “Jiya lokacin da kai abincin dare na samu Ataa bata nan har na kawo Husna na koma bata dawo ba, na tambayi Laraba tace min bata san inda take ba, sai na hankali ya tashi na zata ko Muhseen ya fita da ita ko kuma Doc Bukar domin shi ma kamar yana dan rawar kafa akanta, amman na fara zuwa gidan da na dauko ta na fara dubawa ko taje daukar wani abun kamin na kirasu, sai na same ta tana bachi bakin kofar dakin na kwano, na ji tsoron tashin ta saboda kar ta min masifa so i decided nai gadinta saboda ina jin kamar idan na barta a nan wani zai iya zuwa ya yaga mutuncinta, da daman na mota ya ishe ni sai na fito gurin kwanon na zauna a kasa na jingina....” Yayi shiru na wani lokaci kaminnya cigaba.“For the first time Momy jiya na zauna akan turda, na ji wani yanayi na dabam da ban taba ji ba, gurin babu ac babu katifa, sai hasken farin wata, garin yayi tsif kamar ba bu mai rayuwa a duniyar nan, Momy abunda na fara tunawa da shi shine kabrina, wata rana zan kwanta kamar haka a cikin kabarina, babu shimfida mai kyau babu gado ko katifa, babu haske sai na aikina, duk wani abun dana tara na dukiya da kawa a nan zan bar shi, zan rayu ni kadai a cikin kabarina” Ya fada idonsa da kwalla Momy ta yi murmushi cike da kaunar danta. “Secondly Momy na ji yadda wandada basa da shi suke ji, na taba kasa na zauna a kai i feel it bata da dadi amman a haka wasu suke kwana a samanta a haka wasu suke rayuwa a cikinta, then i realise there are billions of her da abinci kawai suke nema da muhalli, not like thousands of us da idan muka ga dama ba a Nigeria kwana ba a wata kasar ne, i never thought akwai mutumen da zai iya rayuwa a irin wannan yanayin sai yanzu, i never thought there a alot of homeless people da zasu raba a gidan wani kamar haka sai yanzu, Momy na ji wani a cikina some thing differently, wani abun da ban tana tunanin jin sa ba” Murmushi ne har yanzu a fuskar Momy. “Shiyasa Musulunci ya koya mana taimakon marasa shi, ko abinci ka taimakawa wani da shi zaka samu lada kuma zai jidadi ya rika ganinka da kima, yatsun hannyen mu Allah yayi su dabam balle kuma.mutane, dole akwai mai arziki akwai mai talauci akwai mai tsakiyar shi ba mai arzikin ba kuma ba mai talaucin ba, sai dai abunda aka fi so, arzikin da tsarki zuciya, a lokacin da nake nuna maka kyamar talaka ba abu ne mai kyau ba, sai kake ganin kamar ban fahimta ba ne, saboda Fulani ta nuna maka wata tarbiyar ta dabam wacce ba ita na so na dora ka akai ba, talakawa mutane da ya kamata ace an rikesu an nuna musu kulawa da kauna ko da ko su din basa son ka, ka yi dan Allah shi zai baka lada, a lokacin da mutum yake cikin yunwa idan ka ka bashi abinci zai dauke babban masoyi, wanda yake kishi kuma ka shayar da shi, zai ga ba shi wani mai sonsa a duniya kamar kai, balle kuma wanda lafiya ta gagareshi ka tsaya nema masa ba zai taba mantawa da kai ba, kuma ragowar rabon yana gurin Ubangijinka, akwa su da yawa marasa mayafi lokacin sanyi marasa abincin lokacin yunwa marasa mafaka lokacin damina, abu kadam su ke son samun su yi farinciki, while kai Allah ya hada maka komai arziki ilmi lafiya hankali da komai, wani yana can shi hankali ma yake nema ya samu be samu ba, shikenan kai dan Allah ya hada maka komai sai ka ce ka fi kowa? Wata kila ma mutanen da kake rainawa sune a gaba ranar alkiyama kai kana baya a kaskance kuma shine babban talauci” Ya kawar da fuskarsa yana sauke ajiyar zuciya maganganun Momy sun kara taba zuciyarsa ya karanta ya sani amman ya take saninsa saboda yana jin shi din wani ne, yana jin ya fi kowa kuma babu wanda ya isa da shi saboda yana kudi alhalin dukiyarsa ba komai ba ce a gurin Allah.Momy ta share hawayen da suka zubo mata tana dauko zancen Muhseen. “Dazu Muhseen ya fada min cewar kana takura masa akan Ataa hya fada min sonta yake kuma yana son na shige masa gaba” Aliyu ya kalleta da sauri mamaki a fuskarsa karara. “Muhseen din ya fada miki?” “Eh yace ya fada mata ma” “Me kika ce masa?” “Na fada masa ita yanzu ba soyayya ne a gabanta ba, domin mahaifiyarta babu lafiya, wata kila kalaman nawa ba su masa dadi ba, na tafi kai abincin asbibiti tare da ita ko da na dawo na tarar ya tafi, ni kuma ban jidadin hakan ba” “Miye abun rashin jindadi a ciki Momy? Ai gaskiya kika fada masa mahaifiyar yarinya ba lafiya ban dan rashin tunani ba har ya dube ta ya fada mata yana son ta? Kuma yarinyar nan yanzu abunda take bukata ilmi, bata san komai akan addinta ba, yarinyar da bata iya banbance muharrami da ajnabi, ko mahaifiyarta ta samu lafiya ai ilmi ne first abunda take bukata a yanzu i never thought akwai jahilan mutane irinta Wallahi” “Akwai sosai ma, bara fa take wai kaga ba lallai ne ace tana zuwa makaranta ba,ni kaina na fada masa hakan ne saboda na san be kamata yai mata maganar a yanzu ba, shi kuma be fahimci ni ba” “Babu wani rashin fahimta, taya zai ce yana son yarinyar da be san familynta ba? Kuma yar talakawa kamar wannan ai yasan Mama Fulani ba zata taba Amincewa ba” “Shiyasa yake son ma shige masa gaba, kuma ni mai masa komai ce idan hankali ya kwanta” “Idan tana son sa ko?” Ya fada yana mikewa tsaye domin shi sam baya son maganar ma. “Mi zai sa ba zata so shi ba, miye Muhseen ya rasa?” “Ina abincin yake?” “Yana kitchen” Ficewa yai daga dakin zuwa kitchen din, yana ta tunanin halin Muhseen da son banbancewa idan da haske son Ataa yake ko aa, and if ma son ta yake da gaske ai be dace ya fada mata a irin wannan yanayin.Har ya isa asibitin be daina jin haushin Ataa ba shi ya rasa wace irim yarinya ce da har zata tsaya ta saurareshi, he wonder wace amsa ma ta bashi, yaushe ya fada mata zuwansa a nan ko kuwa tun suna Abuja? Wannan karon ba kamar yadda ya saba shiga dakin ya shiga ba, da sallama ya shiga tsabanin baya da sai dai ya tura kofar ya shiga a haka ba tare da sallama ba. Laraba ta amsa masa Ataa kusa na zauna saman gadon da Nana take tana ta mata fira baki har kunne. Da wani irin far'a marar misaltuwa Ataa ta kalleshi kyau da tai da far'ar data haska fuskarta sai ta tasa gabansa faduwa a karon farko. Ba laifi ya saki fuska sai dai ba sosai ya karasa gurin Nana yana mata ya jiki. “Nana wannan shine Aliyun” Ataa ta fada mata tana nuna mata domin a yanzu shi Aliyun ne ta gama bata labari da kanansa da kuma mahaifiyarsa. “Ba mahaifiyarki ba ce kike ce mata Nana?” “Haka ake kiranta” “Idan haka ake kiranta ke sai ki kirata haka?” Tayi shiru tare da yin kasa da kanta. “Karki sake kiran sunanta ba kyau kiran sunan mahaifiya” “Ba sunanta na gaskiya bane, sunanta na gaskiya Asma'u” Wata uwar harara Aliyu ya watsawa Ataa daman wani bakin haushinta yake ji na rashin dalili. Ko minti goma be yi a dakin ba yace zai ta fi sai Nana ta ce. “Mun gode sosai Ataa ta fada mana yadda kake ta hidima da mu kai da yan'uwanka Allah ya saka da alheri ya kara rufa muku asiri ya tsare ku daga ko wane irin sheri ya kara arziki da wadata” “Amin”Ya amsa har karkashin zuciyarsa ya jidadin wannan adduar kusan a rayuwarsa sai yace be taba samun wani talaka ya masa irin wannan addu'ar ba, ba ma talaka kadai ba, ko mai arzikin dan'uwansa be taba masa irin wannan addu'ar ba. Bayan ya amsa da Amin din ya juya ya fice daga dakin. Yana fitowa daga ward din ya hadu da doc Bukar sama sama suka gaisa da Doc Bukar din har Bukar yake labarta masa yadda sukai da Ataa ranar, a nan Aliyu ya warware masa zare da bawa akan maganar tun daga farko har karshe. “Daman ai na san ba zaka aikata ba, ga shi kuma an yi tiyatar cikin nasara gaskiya Doc Muhseen yayi kokari sosai yanzo in time kuma ya maida hankalinsa kam aikin sosai, Allah ya saka hannu a ciki ba a samu wata matsala ba” Aliyu ya yi shiru be ce komai ba har suka jero suna tafiya gurin motarsa. “Ni Wallahi yarinyar ta ba ni tausayi sosai irin wannan idan mutum ya same ta ai sai ya rike ta amana” Ya fada daidai lokacin da Aliyu ya bude motarsa zai shiga ya zauna, kallonsa Aliyu yai sai kuma yai yar dariya mai sauti ya rufe motarsa ba tare da ya ce komai ba, Doc Bukar din ma dariya yake domin shi har ga Allah Ataa ta masa duk da kasancewar matarsa ma fara ce kuma ba shi da niyar kara aure amman ganin Ataa ya ji yana son ta yanayinta da komai nata sun masa. Sai da Aliyu ya kama hanyar wurno road sako ya shigo wayarsa, yana dubawa ya ga number Rahma. _Aliyu kana ina_ Be bata amsa ba ta sake aiko masa wani. _Naga Amina ta saa shegiyar yarinyar a status dinta daman tana gidanka ko?_ _I Love you_ Shine reply dinsa a gareta yana murmushi. _Kana can gurinta ko Aliyu?_ _I Love You_ Ya sake aika mata da reply. _Daman na sani ai tana nan cikin ranka amana ta za ka ci ko Aliyu_ _I love you_ Ya sake aika mata as reply. _I hate you_ Ta rubuto masa a take, wani kasaitaccen murmushi yai ya kara gudun motarsa yana karba kiran Nasir da ke shigowa wayarsa a yanzu.MUHSEEN POV. A ka'ida sai gobe zai koma Abuja kamar yadda ya siya ticket amman ya kasa hakurin zama gidan na minti talati ma balle har ya sake kwana, a yanzu ya fahimta ba Aliyu ne kawai baya son alakarsa da Ataa ba har da Momy domin a yanayinta da ya gani da kuma irin amsar da ya ji a gurinta yasa shi fahimtar hakan, wata kila ita ma bata son ya so Ataa saboda dan ta yana sonta, wanda yake ganin hakan kamar nuna masa banbanci ne tsabanin Aliyu da Mama Fulani take nuna masa kauna fiye da Muhseen din da ta haifa. Shi har yanzu be ga laifinsa dan ya nuna son Ataa saboda tana da kyau ba, ya sani musulunci ma be hana a so mace dan kyauta ba, idan kuma har Aliyu zai nuna kebewarsa da ita matsala shi ma din be dace ya kebe da ita ba, domin shi din ma ba ma a sumi ba ne. Har ya isa Kaduna Momy bata daina kiran wayarsa ba shi kuma be daga ba, be ko tsaya kwana a kaduna ba haka ya bi hanyar Abuja, wani bangare na zuciyarsa yana ba shi hakuri akan ya kyale Ataa ya cire a zuciyarsa yayinda dayan kuma ke zuga shi akan idan har ya barta ya nuna Aliyu ya ci galaba akansa kenan kuma be kamata ya kyale Momy da Aliyu yayi musu hallacci ba idan su din ba su masa ba. Ya shiga Abuja late domin uku na dare ta yi, ya dade yana danna horn kamin a bude masa gate din. To his surprise da ya shiga ciki sai ya samu Mama Fulani da Abbah da su Maryam da Rukaiya duka farke har Baby ma sai fira suke ana cikin nishadi. Ba karamin tsoro da mamaki suka ji ba ganinsa, domin ba saka ran dawowarsa yau ba ko dai zai dawo ba cikin dare kamar yanzu ba.“Lafiya ba ku yi bachi ba?” “Muna celebration ne mutumen nan na Nijar da na ke fada maka ya siye kamfanin har an biya kudi kuma ya danka ragawar kamfanin a gurin Abbah ku, har da wasu gyare gyare ma zai yi” Mama Fulani ta fada baki har kunne. “Mashallah abu yayi kyau Abbah congratulations” Ya mikawa Abbah hannu sukai shaking. “Congratulations to us, Muhseen ya za ka biyo hanya a dare nan? Lafiya dai?” “Ba lafiya ba Abbah amman da safe za mu yi magana” A take murmushi da murnar da ke fuskarsu suka gushe. Bama kamar Mama Fulani da bata son damuwar yaranta. “Ka fada mana ko minene a yanzu ba sai da safe ba, ba za mu iya jira ba” “Ki bar shi idan ya huta da safe sai mu ji ko mienene tashi kaje dakinka” “Na gode Abbah” Ya fada yana mikewa tsaye ya fice daga falon cikin yanayin damuwa. “Ko fada sukai da Aliyu? Ko kuma matar da kaje yi ma aikin ce ta mutu ko wani abun ya faru ba” Maryam da Rukaiya sun fada. “Ko ma minene za mu ji da safe, ku tashi muje ku kwanta” Abbah ya fada yana mikewa tsaye ya fice daga falon zuwa part din Ammy. Lokacin daya shiga part dinsa wanka fara yi yai sallah isha'i da samu yi ba sannan ya saka kayan bachi ya hau saman gadon ya kwanata. Kasa bachi ya yi sai juyi yake akan gadon, duk wani so da yace yana ma Ataa a da sai a yanzu ya gane wasa ne, domin a yanzu ne yake jin matsifar son ta cikin ransa da kuma tsanar Aliyu, tabbas ba zai iya yafewa ta ba, domin a yanzu na gane duk na da ma wasa ne yanzu nen yake sonta da gaske. Kamar kar Aliyu ya fadi cewar yes son ta yake sai ya ji ya kara tsanar Aliyun son ta kuma na karuwa a ransa. *Khadeeja Candy* *ZAKI By Khadeeja Candy 35... Ya farka da wuri saboda be samu kwanan ba har garin Allah ya waye, bachi barawo ne amman ya san wanda yake sata, akwai gajiya sosai a tare da shi amman ko da wasa bachi be ziyarci idonsa ba. Bayan sallah asuba ya dawo dakinsa ya zauna, idonsa na masa nauyi na rashin samun bachi da be yi ba jiya, a yadan bangaren kuma tunanin Ataa ya cika masa zuciya, baya jin zai iya janye ya bawa wani damar daukarta a matsayin mata bayan shi ya fi kowa cancantar wanin ma kuma Aliyu. Idonsa sun yi arba da mata masu kyau masu aji masu natsuwa da hankali ya so mata da yawa saboda kyau amman be taba ganin wacce hankalinsa ya kwanta da ita kamar Ataa ba, kyauwonta ya dauki hankalinsa sosai kusan duk mace daya hadu da ita da kuma wandanda yai so a haya har Mama Fulani tana ce masa ya cika ruwan ido, be taba jin son wata kamar Ataa ba, wani bangare na zuciyarsa yake jinta dabam, ta ina ma zai iya yafe ta a zuciyarsa idan har ya yarda yace zai yafeta hakan na nufin ya zama ragon maza kenan. Kurciyarta mu'alamarta kyauta na daga cikin abunda yasa yake son Ataa. Da gangan yai zamansa ya ki fita ya karya bangaren Mama Fulani kamar yadda ya saba, ya kwanta a cikin dakinsa ba dan kuma yana jin bachi ba sai dai Mama Fulani ta fahimci cewar yana cikin damuwa, domin ya san matsalarsa ba karama bace a gurinra yadda take tsanar talaka ba zata amince ya auri Ataa ba, balle kuma Ataa din da ta tsana tsana ta musamman. Maryam ce ta shigo part dinsa ta tsaya daga bakin kofar bedroom dinsa tana kiran sunansa. “Ya Muhseen Mama ta ce ka fito mu yi breakfast” Na tare daya juyo ya kalleta ba ya ce. “Bana ci” Juyawa tai ta koma ba sai ga Mama Fulani ta shigo dakin hankalinta a tashe.Saman gadon ta zauna ta kai hannun tana tashinsa domin ya bata baya ne. “Muhseen lafiya kake?” Juyowa yai yana kokarin tashi zaune kallonta yai idonsa sun kade sun yi ja fuskarsa ta dan kumburo saboda ciwon kan da yake ji da kuma bachin da be samu yi ba. “Mama ina kwana?” “Lafiya Kalau Muhseen mi yake damunka?” “Ba komai kaina ne kawai ke ciwo” “Ba wani ciwon kai daga ni har Abbah ku jiya da tunaninka muka kwana, ka dawo cikin dare a yanayin da kowa ya ganka ya sam akwai abunda yake faruwa, yau kuma baka fito cin abincin safe ba na aiko Maryam ta kira ka ce wai baka cin komai, yanzu kuma ka fada min babu komai?” Kallonta yai “Mama ko na fada miki damuwata ba daukarta za ki yi da muhimmanci ba, ba lallai ne ki min maganin matsala ta ba” “Mi zaka nema a duniyar da ba zan maka ba Muhseen? Kai fa da na ne karka manta wannan, matukar ina da yadda zan yi to zan maka ka samu ko mi kake so a duniyar nan” Yaja wani dogon numfashi ya sauke. “Kamin na fada miki damuwata ina son nai miki tambaya” “Minene?” “Mama ba dan ina danki ba, ina son ki fada min gaskiya shin ina da wani nakasu ne da zan ce ina son wata a hana ni? Ba ni da abunda ake so a namiji ne ko kuwa tarbiya ce bata wadace ni ba?” “Babu, babu wance zaka furtawa so ta ki karba maka Muhseen babu ta babu abunda ka rasa a cikin abunda ake so a gurin ďa namiji, fada wace yarinya ce ta tashi hankalinka haka? Wa kake so Muhseen? Zan nema maka ita ko yar idan shugaban kasa ce” “Mama Momy ta Aliyu sun bata ni a gurin yarinyar da na ke, saboda suna min kallon mazinaci alhalin ban taba aikata alfasha ba a rayuwa Allah shine shaida ta” Kallonsa Mama Fulani take tana son tantance abunda ke fitowa daga bakin ďanta. “Wa kake so Muhseen?” “Ataa Mama Ataa” Ya bata amsa kai tsaye yana wani marairaicewa. “Momy da Aliyu sun yi min daidai, suna nuna maka, hanya kana cewa ba haka ba, sai yaushe zaka level dinka dana yarinyar nan ba daya ne ba? Sai yaushe zaka daina yaudarar kanka? Ka rasa wacce zaka so sai yar talakawa yarinyar zuri'ar kaskantattu, Aliyu ba kamako ba ne irin ka shiyasa ya ke nuna maka ka daina son ta kana ganin kamar takura maka yake amman matsayinka da na yarinyar nan ba daya ba ne Muhseen” “Miye banbanci na da ita Mama? Talauci? Saboda ita yar talakawa ce ko? Idan har wannan ne kawai miyasa shi Aliyu yake son ta kuma Momy ta goya masa baya?” “Aliyu ba zai taba son wannan yarinyar ba har a bada, Aliyu ya san abunda yake ba shashasha ne kamar kai ba, ba dan wannan abun daya faru ba ina da tabbacin Aliyu ko a hanya ya hadu da ita ba zai taba bata sadaka ba ma balle har ya taimake ta, kuma ka jira ka gani yana gama taimakonta zai watsar da ita” A fusace Mama Fulani take wannan maganar ta juya zata fice Muhseen.“A niyarsa ta watsar da ita yasa ya dauketa ya kai ta gurin Momy ko? Aka sama mata daki a cikin gidan, suka sauke ta a ciki aka bata gurin waka da tufafi, ana kula da mahaifiyarta, idan ba sonta yake ba mi zai saka yayi mata duk wannan Mama? And if ba kaunarta yake na mi zai saka Momy bata ba ni goyon baya ba?” “Ba zata taba baka goyon baya ka auri yar matsiyata ba, yarinyar da ba a san asalinta ba, wata kila ma dangin mayu ce ta tafi da kurwarka tana can tana azzabtar da kai shiyasa kake ta haukan son ta, daman buzayen nan ba su aje komai ba sai bakar maita, Aliyu yana nuna maka abunda kake ba daidai ba ne kai kuma ka saka fahimta, kuma bakinka ya daina furta son wata yar talakawa ga Aliyu har abada Aliyu ba zai taba son Ataa ba ba kuma zai taba son wata banza kamar ta ba, ni na raini Aliyu tun yana karami har ya girma na san waye ďana tir Aliyu ya so Ataa balle har ya aureta” Ta fada tana tofar da yawun bakinta sannan ta fice daga dakin tana kara fadin. “Ka mutu indai akan Ataa ne” Wani irin Muhseen ya ji kamar an saka takobi an fasa kirjinsa an fiddo zuciyarsa an raba ta gida biyu. A take kan ya kara safa masa, daman ya san Mama Fulani ba fahimtarsa zatai ba, ba kuma shige masa gaba zatai kamar yadda ya so ba, ba dan komai ba sai dan ta tsani talaka, kwantawa yai saman gadon ya rumshe ido kamar mai bachi yana jin yadda zuciyarsa ke masa mugun zafi. A fusace Mama Fulani ta dawo part dinta har wani huci take saboda bacin rai. “Mama Lafiya?” Rukaiya dake falon ta tambaya. “Wai ni Muhseen zai kalla ya fadawa yarinyar can Ataa yake so bayan na gargade shi akan kar ya sake kula ta?” “Ataa kuma? Yana nufin saboda ita ya shiga damuwa?” “So yake yai hakan saboda na tausaya masa ni ko mutuwa zai yi ba zan taba bari ya auri wannan yar iskar yarinyar ba, wai har wani cewa yake Aliyu ma son ta yake Momy ta goya masa baya” “Taf Ai Wallahi Ya Aliyu ba zai taba son ta ba son ta ba, idan ma ya ji Ya Muhseen ya wannan maganar sai sun samu matsala da shi” Cewar Rukaiya tana kai bread a bakinta. “Shine dai dan ya ganta yana son ta sai ya dauka kowa ma son ta yake, maganar Maryam ce kyau nn ne yake dibarsa”“Ni wannan yarinyar zuwanta gidan nan ya zame mana fitina, daga ganinta shi da Kamal har da Ya Aliyu ma suka haukace” “Kaddara ce ta saka aka kawo min ita daman, ba zan sake daukar ko wace yar aiki ba, dan nan gana sai a a kawo wacce Abbah ku zai gani yace ita yake so ma, shi kuma Aliyu bar ni da shi har wani sauke ta gidansa yake” “Wata Momy ce ma ba shi ba, kin san halin Momy Allah yayi ta da son jan mutane a jiki ko tsoro bata ji” “Ai zan kira shi sai na saka ya dauke ta daga cikin gidan nan, idan mai kyau Muhseen yake so ya koma tsason mu mana, akwai kyaun da ya wuce yayan fulanin asali ma, wannan da ba a san inda ta fito ba ni abun nan har mamaki yake ba ni wallahi, mtssss” Mama Fulani ta fada hakan tana nufi dakinta har yanzu bata daina jin haushin maganar da tai da Muhseen da ta sam tun farko abunda zai fada mata kenan da bata dame kanta da son sani ba, ita dai bata da wani abun a gurin Ataa ba, ta san tana da kyau amman a gurin ko kafi kowa kyau a duniyar matukar baka da nera ko kuma kai ba dan kowa bane, biri ya fika a gurinta indai har birin nan yana da masu gida rana. Bayan fitar Mama Fulani dakin ya sauka daga kan gadon ya nufi gaban madubinsa ya tsaya yana ta kallon kansa, a zahiri kansa yake kallo amman a badini tunanin mafita yake, har ga Allah yana son Ataa shi a yanzu ma yaji yana bukatar aure daman rashin samun wacce tai masa ne yasa shi be maida hankali gurin auren ba, amman yanzu ya yana jin son aure sosai a ransa, kuma yana matukar jin kaunar Ataa a ransa. “This is the right time daya kamata nai fighting akan abunda na ke so, this is the right time da zan tsayawa kaina da kaina, ba zan iya barin wannan ta wuce ni ba, idan har ba zata so ni to be kamata ta so Aliyu ba, idan har zan iya hakura na kyaleta to ko ba sonta na ke ba” Magana yake da kansa yana kallon madubin dakinsa, yana jin wayarsa na ringing amman ya ki ya duba mai kiran ma balle ya daga. Bathroom ya shiga yai wanka yana fitowa ya shirya cikin kananan kaya sannan ya dauki wayar yana duba miss calls din da Momy ta jera masa, kiranta yai da dayan layinsa da be cika kiran mutane da shi ba. “Momy ina kwana?” “Lafiya Kalau Muhseen, miya nai ta kiranka ka ki ka daga? Kuma ya wuce na tare da ka min sallama ba?” “Kawai raina ne ya bace, amman ki yi hakuri dan Allah”“Ranka ya bace saboda na fada maka gaskiya Muhseen? Har ga Allah yarinyar nan yanzu ba soyayya ce a gabanta ba, bana jin ta san wani ma wai so, ta mahaifiyarta take shiyasa ban goya maka baya ba, komai ai dan a hankali ne” “Ba abunda kike ce min ne kawai ba Momy, har da yanayin da na ga Ataa din wata kila wani abun Aliyu yace mata a kaina domin na ga tana daridari da ni ba kamar da ba” “Idan ma wani abun ya fada mata ba damuwana ba ne, kai na ke son ka kwantar da hankalinka idan komai ya daidai kai kanka ka sani ni mai nema maka auren yarinyar nan ce tun da har ka furta kana son ta” “Na gode Momy, amman Mama ma bata so ta min fada sosai yau saboda Ataa tana ganin kamar be dace na aureta ba, jarabawa ce kawai Momy kuma na hakura da ita” “Haba dai, wane irin ka hakura da ita kuma? Fulani uwa ce kawai ba uba ba, ba ita zata maka aure ba, kuma zan tattauna da ita amman sai hankali ya kwanta komai ya daidai ta na maka alkawari” “Na gode sosai Momy” Daga haka ya sauke wayar a kunnensa ya saka aljihunsa ya dauki abubuwan bukatarsa ya fice daga dakin. ALIYU POV. Da yamman ya koma gida ba dade wurno road din ba saboda ya san ran matarsa yana can a bace. Kamar wanda aka koro haka yai fakin a cikin gidan ya fito da sauri ya shiga cikin falon. Kai tsaye dakin Rahma ya wuce ganin bata falo sai ya samu a dakin ma bata nan, be kawo cewa tana dakinsa ba domin ba ta cika shiga dakinsa idan baya ciki ba, sai ya sauko ya leka kitchen be same ta a nan ba, tunani daya ne ya zo masa arai wata kila ga hi fushi ta tafi gidansu.Remote ya dauka ya kashe tv falon sannan ya nufi dakinsa yana bude batulan rigarsa. To his surprise yana shiga dakin ya same ta zaune kasa kusa da bed dinsa tana hawaye. Cikin sanyin jiki ya karasa kusa da ita ya zauna yana kallon fuskarta. “Minene Rahma?” Dagowa tai ta kalleshi tana hadi yawun bakinta idonta yayi ja sosai alamar ta dade tana kukan kenan. “A daina kula da ni a yanzu, da a da nd da kanka zaka dawo ka ba ni magani ko ka kira waya ka tambaya idan na sha amman yanzu baka damu ba, ka canja Aliyu ka tashi daga sanin da nai maka zuwa wani dabam, babu ruwanka da matsala a yanzu, da a da ne ba zaka iya zuwa ka kwana wani gurin da ba kusa da ni ba, idan ko har ba kusa da ni ba to a gida zaka kwana ba wani gurin ba, ka kwana a gida ka bar matarka ta sunna saboda wata matar da baka san inda ta fito ba, kana tunanin ka min adalci kenan?” Hannunta ya kama ya rike yana matse shi cikin hannunta. “Na sani wata zan zama babu ni, ina kawo abubuwa da yawa a rai, kamar samun lafiyata a can baya, yanzu kuma mutuwa ta, samun haihuwa wata rana da kuma dawwama a haka, amman ban taba kawowa cewa zaka so wata macen bayan Rahma ba, amman na ga ni ba ma ji nai ba, ba zan iya dawainiyar kishi a yanzu ba Aliyu idan har ka fara son wata ka sallame ni ka ji da ita ni kuma na ji da ciwo na, na sani ka yi kokarin zama da ni, amman idan ka yi hakuri wata kila ba zan dade ba zan tafi na barka sai ka auri wacce kake so, na kasa fadawa iyayena matsalar nan tun bayan wacan matsalar da muka samu na san idan har na fada musu za su nemi raba aurena da kai, saboda gudun bacin raina, amman bana son aikata hakan ya zama kamar butulci a gareka na san zaka kalli cewa iyayena ba su kyauta maka ba...” Matsawa yai kusa da ita ya jata jikinsa ya rumgume.“Babu kowa a cikin zuciyar Aliyu sai Rahma, ke kadai na ke so Rahma ban daina son ki ba kuma ba zan daina ba har abada, ba wai na gaji da dawaniya da ke ba ne, wannan dawainiyar da ke da yarinyar nan ma saboda ke ne, duk wani hali da yarinyar nan ta shiga saboda ke ne, bayan tausayinta da tsoron ta shiga wani hali babu komai a zuciyata, ba son ta na ke ba Rahma” Dago kanta tai ta kalleshi. “Amman Aliyu saboda ita ka zo nan ai, kuma tana gidan Momy kana kula da ita” “Momy ta sauke ta gidanta ne saboda ba su da wani gurin zama a yanzu, idan aka barta ita kadai zata iya shiga wata rayuwar dabam, ba saboda ita kawai na zo nan ba har saboda ke kin sani Rahma ina kauna sosai mi zai saka ki tashi hankalinki?” “Aliyu kana da kyau da siffa mai kyau ba ko wace mace ce zata daga maka kafa ba, balle kuma ace kai na nuna mata so da kanka, ina kishin ka so wata Aliyu ina jin zuciyata kamar zata fashe ina jin duk ranar da ka auri wata mutuwa zan yi” Ta fada tana kamkameshi kamar zata shige cikin jikinsa. Wani kalar tausayin matarsa ne ya lullube shi shi kansa ya san be kyauta mata ba, ya kwana wani gurin bayan ita tana gida tana sammanin dawowarsa. Saman kanta yai kissing yana shafa bayanta. “I'm sorry” “Yanzu yarinyar tana ina? Gidan Momy ita da mahaifiyarta ko? Ta tare a can so that ka rika ganinta tana jindadi ko? Na sani ai tana son ka, dole ai zata so ka” “Yarinyar nan ba son kowa ne a gabanta ba, mahaifiyarta na asibiti tana jinya? Hankalinta yana gurin mahaifiyarta ne” “Wace asibiti?” Be amsa ta ba, ya cigaba da shafa bayanta, ita kuma bata sake tambayar ba, bata bar jikinsa ba sai da aka kira sallah magariba. Sannan ya daga ta daga jikinsa ya shiga bathroom yai alwala, tana ganin ya shige ta yi saurin mikewa tsaye ta nufi dakinta wardrobe ta bude tana duba kayan cikin ba dan zata saka ba sai dan ko shigowa yai ya tararda ita tana wani abun. Be shigo dakinta ba sai dai ta ji lokacin daya sauka kasa ya bude kofar falon ya fita. Gurin windows ta koma tana lekensa, hangoshi ya fita ba tare da mota ta san ba zai je nesa ba wata kila da yayi sallah zai dawo gida. Dawowa tai ta dauki wayarta ta turawa Muneera sako sannan ta goge ta shiga bathroom din dan yin alwala.ATAA POV. Mun wuni da Nana tana ka ce bakinta, muna ta fira kamar ba rashin lafiya take ba, a yadda na ke ganin ta samu sauki a yau kawai na gode Allah ba adadi, domin idan abun ya daure a haka Nana ta dauko hanyar samun sauki fiye da wacan aikin da aka mata a asibitin Asim. Sai dai hakan be hana na wuni da rashin jindadi kalaman Muhseen na bankwana a gareni ba. Da dare Husna da Siyama suka kawo min mana abincin dare sosai suka so na bi su zuwa gida amman na ki, ko ba komai na san Nana zata fi sakewa idan ta gan ni zata fi sakewa ni ma kuma hankalina zai fi kwanciya idan ina ganinta duk kuwa da na san ba wani maganin zan iya mata ba. Ni da Laraba muka ci abinci dare a ranar, sannan muka kwanta a Bedsheet daya Nana kuma tana saman gado, bachinta take da ninshari har garin Allah ya waye. Asubar fari aka tashe mu ni da Labara masu wankin daki muka fito waje sai da aka gyara duka ward din sannan muka dawo. Na yi zaton Aliyu ne zai kawo mana abun kari sai naga Husna da Siyama kamar dai jiya, bayan sun yi ma Nana ya jiki suka dauki kulolin jiya suka koma da su, haka nai ta rabon ido da rana ko Aliyu zai dawo amman be dawo ba, sai direban gidansu aka aiko da abincin rana ya kawo mana. Bayan wucewar direban tare da Labara dan tace zata fara zuwa gida ta gyara idan ta dawo sai ni na tafi na shirya. Nana na fara zubawa shimkafar da miyar ina ta bata tana ci a hankali har ta koshi na bata ruwa ta sha sannan na zubawa kaina na ci sai da na koshi sannan na zuba lemu na sha. Ina aje kofin wani mutum mai kamar masinja ya leko dakin mu.“Wai ance ana kiran Ataa” “Wa ke kirana?” Na tamabaya ina tashi tsaye na bi bayan mutumen da ya riga da ya fice. Hango inda ya bi yasa na bishi har muka isa wani dakin da nake zaton dakin likita ne muna shiga ciki zaton da nake ya zama gaskiya, domin kuwa dakin likitan ne sai dai macece tana hakimce saman kujerarta tana kallon laptop din gabanta tana murmushi. “Hajiya ga nan” Mutumen ya fada sai tai masa alama da ya tafi ni kuma ta nuna min kujera, bayan na zauna ya dauko wani katon wali ta miko min, sannan ta juyo da laptop din gabanta izuwa inda nake, Muhseen na gani a ciki yana zaune saman wata kujera mai juyawa da alama shi ma yana office din ne. Matar ta tashi ta fice daga dakin ta barni da laptop din da kwali a hannu, ban dauka da gaske na ke ganinsa a ciki ba har sai da yai min magana. “Pretty ya jikin Mamana?” Ya dan wara ido kamin na amsa masa. “Jiki Alhamdulillah, da gaske kai ne?” “Yes ba gani kina ganina ba, ta ji sauki sosai?” “Eh bata manta komai ba” “Ina iya kokari na hada da addu'a a gurin aikin dan an samu na yi aikin cikin nasara, na san yadda uwa take da muhimmanci musamman ke da kike bukatarta, ina son ki rayu da mahaifiyarki duk kuwa da kin nuna min ba kya so na, amman ba son ne a gabana ba samun lafiyar mahaifiyarki ne a gabana” Ya fada yana murmushi ni kuma na yi kasa da kaina ina taba kwalin dake saman cinyata. “Ataa.... ” Na dago na kalleshi. “Bude kwalin” Na bude kamar yadda ya bukata wani kyakkyawan zobe na fara cin karo da shi, a kasanshi kuma cake mai zagayen zuciya. “Ban san size din yatsunki ba amman na san idan be miki yawa ba, ba zai miki kadan ba”“Zoben minene?” “Na zinari ne” Wani tsoron na ji na kamani daman tunda naga yanayin zoben ma dauka cewar na zinari ne, sai dai rashin ranin hakikanin zinarin yasa ban yi saurin yake hukunci ba har sai da ya fada min. “Ni ban taba saka zinari ba” “Kin fara kenan daga yau, ke din ai matar manya ce Ataa, ba dan ina son ki nake son ki saka zoben ba, sai dai kar ki manta da ni, a duk lokacin da kika tuna da samun lafiyar Nana ki min Addu'a Allah ya bani mata irin ki” “Amman....” “Karki ce komai Ataa pls ki saka dan Allah” Akwa girma da nauyin a hada ka da Allah kuma ka saka yin abun nan, ko be hada ni da Allah ba mutumen da yai ma mahaifiyata tiyata ta samu sauki ya cancanci ya saka wani abun nai masa balle kuma ya hada da mahaliccina. Bude akwatin zoben nai ya fiddo daga ciki, sai da na kalli Muhseen sannan na saka zoben ina hade yawu gabana na bugawa da mugun karfi. Wani irin abu na ji ya ratsa ni, wata irin daraja da daukaka suka cika min ido, saurin cire zoben nai hawaye na sauko min. “Ba zan iya sakawa ba Muhseen ka yi hakuri” “Ba zan cilasta ki ba Ataa amman ki aje shi a gurinki” Na gyada kai kamar yana gabana ina share hawayen. “Upper week zan zo na yi ma wasu aiki, fada min abunda kike son na zo miki da shi, Mama Fulani ma ta ce na tambaye ki abunda kike so na zo miki da shi” “Ni” Na fada ina nuna kaina da tsananin mamaki. “Yes baki yarda ba? Idan na koma zan fada mata ta kira ki da kanta” “A a karka ce karka saka ta” “To fada min abunda kike son na kawo miki” Na yi shiru ina nazarin ban san mi zan ce masa ba. “Kina son turare?” “Eh ina so”Na amsa da sauri domin ya fanshe ni daga dogon tunanin abunda zan fada. “To zan kawo miki, ki ci cake din kin ji?” Na sake gyada masa kai ina kallon yadda yake kurba tea da ke gabansa. Murmushi ya sakar min kamin ya kai hannunsa ya taba wani gurin sai hotonsa ya bace bat. Mikewa nai tsaye ina rike da zoben da kuma cake din na fice daga dakin. Kadan kadan nake tafiya ina jim kalamansa kamar yanzu yake fada min su cewar Mama Fulani tace a tambaye ni abunda nake so, yafi komai bani mamaki da al'ajab, anya da gaske ma tace haka ko kuwa cewar Muhseen ne. Da wannan tunanin na shiga dakin da Nana take ina shiga na samu wata mace a tsaye tana sanye da yadi maroon da garin gyale, daga ganin yarinyar ka san budurwa ce ko da ganinta zata yi masifa. “Ke ce Ataa?” Ta tambaya tana zare min ido, gabana ne ya fadi har na kasa amsa mata na gyada mata kai kurum. “To ki fita daga hanyar Aliyu domin ba makaskanci ba ne irinki, Aliyu ya fi karfin ko wace mace balle kuma ballagaza talaka irinki, yar bara a titi marar daraja....” Yarinyar bata gama fada ba Nana ta daka mata tsawa da yaren buzanci tana zaburowa kamar ba tiyata ce a jikinta ba. “Ke ya ishe ki” Saurin karasa nai gurin Nana na dafata ina rufe mata baki. Sai yarinyar ta juyo ta kalli Nana ta ce “Aniyar da biki idan ma wani abun ne kike karantawa ni na fi karfinki da duk danginki, kuma Wallahi Aliyu ma yafi karfinku duk wani abu yana muku shi a matsayin taimako amman shi kansa baya son kaskantacin mutane irin” Mikewa nai tsaye ina nuna ta da yatsa na ce. “Ke ce kaskantacciya domin da kina da wani matsayi a gurin Aliyu da kin hana shi taimakon ku ba sai kin zo kina mana ihu a cikin asibiti ba, jahilar banza wacce bata san darajar dan adam ba.... ” Matsuwa yarinyar tai ya wanke min fuska da mari ta buge kwalin da ke dayan hannuna da zoben suka watse kasa. “Lalala wato har da su zobe ya baki eh lallai zaki ci ubanki” Ta nufi inda zoben yake ta dauka ni kuma na yi kanta na rama marin da ta min ina kuka sai juyo ta rikani ta buga da karfen gadon da Nana take kai a take kaina ya fashe da jini ya fadi zaune a gurin ina kuka, ita kuma tai ficewarta tana kwafa. ZAKI By Khadeeja Candy 36... Ina zaune a gurin ina ta aikin rare kukana a hankali marar sauti sosai Nana na samam gadon ita tana hawaye, jini nata min zuba sosai har jiri na ke gani na kasa tashi a gurin kuma na kasa daga muryata na waje ya ji ya kawo min taimako. Sai bayan sallah la'asar Laraba ta dawo dakin tana ganin halin da nake ciki ta bugawa Momy a waya ta sanar da ita cikin tashin hankali. Ba a dauki lokaci ba Momy ta iso asibitin ina da Amina, tana ganin halin da nake ciki hankalinta ya tashi da sauri ta rikani ta fita da ni zuwa inda za a wanke min ciwon. A gaskiya ta nuna min kulawa sosai bayan sun wanke gurin suka ba ni magani ta biya kudin komai, ba ta dawo da ni dakin da Nana take ba, sai ta nufi motarta da ni, tana rike da ni har muka isa a gidan baya ta saka ni ita kuma ta shiga a front seat Amina ke tukawa, tun kan mu isa ta kira wayar Aliyu ta fada masa tana nemansa cikin fushi. Da muka isa sai ta wuce ciki Amina ce ta rika ni muka shiga ciki, a saman kujera ta zaunar da ni ta cire min hijab babu nuna kyama ko gazawa a tare da Amina da mahaifiyarta, ruwa Momy ta ba ni mai dan zafi da lemun tsami a ciki a na sha sai ta dauki kofin na kwantar da kaina saman kujerar na lumshe ido ina sauraren yadda take fadawa su Husna da Siyama abunda ya faru cikin fada kamar yarta a aka taba.Mutanen nan biyu sun koya min wani darasi na rayuwa, kyamar talaka da Mama Fulani da 'ya'yanta da suke ra'ayi ne kawai na kansu ba dan talakan ya musu wani abun ba. So da kauna da kulawar da Momy ke nuna min ya karantar da ni wani halin dabam na dan adam. Momy ma masu arziki ne sosai amman bata taba nuna min kyama ba, ta san darajar talaka ba dan zata amfana da ni ba, sai dai tausayi da jin kai da ya cika zuciyarta, halin ne na dan'adam wani da dadin zama wani babu, wani da sanin darajar dan'adam wani babu, haka rayuwar take tafiya kowa da irin ra'ayinsa da halinsa da kuma tarbiyarsa, domin kuwa Husna da Siyama da Amina suna bin tarbiyar da Momy ta dora su akai ne, yayinda Yayan Mama Fulani suke bin tarbiyar da ta dora su akai, ban ce Muhseen da yake da wata rayuwar ta dabam wacce ta fidda shi dabam a cikin yayanta, yatsun hannunmu ma ba daya bane ta ita halin kowa zai zama daya. Ina kwance na a gurin na ji kamshin turaren Aliyu wani irin turare mai kwnatar da hankali da saka nishadin ruhi, ina jindadin shakar kanshin sosai fiye da komai a yanzu. Da sallamarsa ya shigo Momy ta ki amsa masa sai Husna ce ta amsa masa wanda hakan ke nuna cewar Momy tana cikin fushi sosai, tashi Husna tai ta nufi kitchen daman ita kadai ta rage a falon Siyama da Amina tuni suna shiga dakinsu dan yim wani sha'anin. “Aliyu ka fadawa Matarka cewar kana son Ataa ne?” Kallonta ya tsaya yi kamin ya tantance abunda ke fitowa daga bakinta. “Son ta kuma? Kamar ya?” “Wata taje ta taki akanka ta fada mata cewar idan bata fita daga sha'aninka ba sai ta mata illa, ta mareta kuma ta fasa mata kai” “What” Ya furta yana karasowa zuwa inda na ke ya duba kan nawa, tashi nai zaune ina kallon yadda fuskarsa ta canja ganin bandeji a goshi idona har ya kumbura saboda kukan da nai na gaji.“Ba zai yiyu ba, yarinya kamar wannan ace zata sake shiga wani halin kuma, ta wanne zata ji da jin mahaifiyarta ko da kishin matarka? Kishin ya kai har ta saka aje a fasa mata kai? Wannan wane irin rashin mutunci ne? Idan ma sun ta kake yin hakan zai saka ka fasa ne? Shi kenan dam tana talaka ba da daraja da kima a gurinku? Idan yar wani Minister ta ce Rahma ta isa ta dake ta ma balle har ta nuna mata yatsa? Da ace ita ce ta yi ma Rahma haka ina da tabbacin yau Ataa a gidan yari zata kwana saboda ta taba yar gata, to ya bata fi ya ba Rahma dan ta tana yar masu arziki bata fi Ataa ba dukansu mutane ne, suna zamansu lafiya cikin rufin asiri za su tashi hankalinta da na mahaifiyarta, ita Rahma idan mai tunani ce ai kamata yai ta kama Ataa ta rike ta martaba ta kodar mahaifiyarta ce a cikim cikinta fa, tasan bata da lafiya idan Allah ya ga dama sai ta fadi ta mutu a take amman sai neman wulakanta wata take? Idan ma son ta kake ta isa ta hana ne? Wallahi ka jawa matarka kunne idan ba haka fadan a tsakanin mu zai dawo domin ba zan zuba ido su cewa Ataa mutunci ba, idan ma ai kake goya mata baya to ko kuma ka kwashi matarka ku koma can Abuja.....!” Tana kawai nan ta tashi a ficewa ta nufi dakinta ba tare da ta tsaya sauraren abunda Aliyu zai fada ba. Tun da take fadan na ke kallonta ina hawaye cike da kauna marar misaltuwa, wata uwa bata taba tsaya ta shigar min fada ba bayan Nana amman a yau na samu wata mace da ta rike ni 'ya har ta take fada da danta akan abunda surukarta tai min, ciwon kan da zazzabin da suke son rufe ni a take na neme su na rasa, wani irin kaunar Momy ya cika min zuciyata, hakika ta uwa Momy uwa ta gari ce mai iya kula da yayan kowa kamar yayanta. Risinawa Aliyu yai gabana yana kallon fuskata a hankali ya shiga min magana. “Sannu” Na gyada masa kai tare da saka hannu na share hawayena. “Wacce ta dake ki cewa tai Rahma ta turo ta?” Na girgiza kai. “Bude ba ki yi min magana mana” Kasa nai da kaina haka nan kawai na samu kaina da kasa bude baki na ce masa komai har na tsawon lokaci. Tashi nai tsaye na soma takawa da zimmar shiga bathroom din Amina saboda fitsarin da suka cika min mara, sai na ji ya kira Husna da ke kitchen ta fito da sauri. “Rika ta ki kai ta daki” Sai da ta kalleshi sannan ta zo ta rika ni ta nufi dakinta da ni a maimakon dakin Amina.“Kwantawa za ki yi?” “A a fitsari zan yi” Bandakin ta nufa da ni sai da muka shiga ciki sai ta fito, bayan na gama abunda zan yi na fito sai na zauna kasa na jingina da gadonta, murmushi na ke abunda Momy ta yi min ya faranta min rai sosai, Husna na shigowa dakin ta saka na tashi daga kasa na koma saman gadonta na kwanta, nan da nan bachi yai gaba da ni. ALIYU POV. Da kallo ya bi Ataa wance Husna ke rike da ita har suka shige dakin. Yana ta mamakin abunda Rahma tai bayan yau da ita ya wuni saboda ita ne be je ko'ina ba. Mikewa yai tsaye ya fice daga falon zuwa motarsa, yana shiga ya dauki hanyar gidansa. Harabar gidan ya faka motarsa yana kallon wata bakuwar mota da ke fake a gafen ta Rahma, ya fito yana rike da keys din motarsa a hannunsa ya tura kofar falon ya shiga. Rahma ya samu zaune ita da Muneera a kujera daya, da alama fira suke yi ko kuma wani abun Muneera take fadawa Rahma sai dai ganinsa ya saka sun yi shiru. “Sannu da zuwa” Rahma ta fada sai yai mata banza ya nufi upstairs. “Ranka ya bace saboda an gargadi wata banza” Ta fada tana mikewa tsaye, shi kuma ya juyo ya kalleta. “Akan me za ki nemi takurwa yar mutane? Ce miki nai ina sonta? And what makes you think abunda kika saka ka mata zai sa na canja na fasa taimakonta ne? Wallahi abunda kika yi be kara min komai ba sai tausayinta, yarinyar da ke jinyar mahaifiyarta saboda ke a maimakon ki tausaya mata ki taimake ta sai neman saka ta kike a cikin wata fitinar, matace ke ina martaba ki ina mutuntaki ba zan bari wani ya zaga miki rigar mutunci ba, kamar yadda ba ba zan bari ki yagawa wani ba wanin ma kuma wacce ta taimake ki rayuwarki” Ya fada cikin daga muryar fuskarsa a hade kamar bakin hadari. “Abunda kake yi abun kunya ne Aliyu namiji mai daraja mai kima da mutumci kamar ka ace yana bibiyar wata banza yar talakawa yar bara a titi wacce bata san mutuncin kanta ba, namiji nawa na kwanta da ita lokacin da take bara baka sani ba, amman abun kunya har ka dauki robe da cake ka bata zobe ma mai tsada wanda na yi imani bata taba ganin irinsa a rayuwarta, ka yi kuskure Aliyu kuma kana shirin aikata kuskure idan har ka ce zaka hada ni kishi da wata kazama wacce ba a san ubanta ba balle asalinta, wannan ne kuskure mafi girma da zaka aikata hada ni kishi da yar talaka, abunda za ka yi ka burgeni ka nemo yar wani minister ko yar wani mai ji da kansa ka hada ni shi da ita amman ba yar iska yar gantali a titi ba, wacce ta kwana a titi yan sanda suka gama amfani da ita Doc Asim ya gama amfani da ita kai kuma yanzu kake son kawota cikin gidanka” Tana fadar hakan ta juya sai Aliyu ya juyo da ita da dukan karfinsa yana kallonta naman fuskarsa har rawa yake saboda bacin rai. “Idan zan so Ataa ba zan so ta dan wani abu nata ba, kamar yadda ke ma ban so ki dan wani abu na ki ko na gidanku ba, ban taba son mace dan wani abu nata ba kin fi kowa sanin wannan” “Ba haka ba ne, ka so ni a yadda na ke saboda ka san cewa baka haihuwa saboda kai juya ne, so that sai mu taru mu mutu a haka, yanzu kuma kana ganin ka gaji da ni mahaifiyarka ta saka ni a gaba shine zaka fara son wata ko? Watan ma yar titi wacce kai da kanka kake nuna mata kyama amman mahaifiyarta take kokarin gyarata saboda kana sonta, daman na sani yan'uwanka gaba daya ba so na suke ba” “Ba ki da kunya Rahma, kina magana kamar ba ki san da wanda ki ke magana ba, mi yake damun ki ne?” “Abunda yake damunka Aliyu, abunda ya saka ka canja ka koma kamar mahaukaci akan wata dabba can, shiyasa na gano matsala da kai idan har zaka iya runtse ido a halin da muke ciki ka ce zaka min kishi to sai an bata guri ta zo ta zauna da kai fa haihu na gani” “Za ki yi nadama matukar kika ce Zabin Rai za ki bi, ina daga miki kafa ne saboda sanin abunda yake tare da ke, ina tausayin ranar da za ki yi nadama Rahma, wulakanta dan 'adam ba shi da kyau musamman wanda ya taimaki rayuwarka” Wani kallon mamaki tai masa “Haka ka fadan to sai kaje ka aureta ka zauna da ita, daman ai haka halin ku maza yake” Ya nufi hanyar dakinta a fusace tana wugar da zoben.Aliyu ya juyo gurin Muneera ya kwada mata mari mai kyau sai da ta jishi har cikin kanta. “Karki sake zuwa ki ce za ki taba yarinyar mutane, duk wani abu a tsakanina da Rahma ne babu ruwanku a ciki” Ta dafe kuncin hawaye na sauko mata tace. “Saboda wata banza yar talakawa za ka mare ni Aliyu?” Kara mata marin yai a dayar fuskarta sai ta hada hannu biyu da dafe fuskarta tana fashewa da kuka. “Talaka ai ta muku rana, ko ba kodar talaka ce a jikin yayarki ba? Ku ba ku san darajar talaka ba amman kun iya wulakanta shi? Bana son wuce gona da iri, ki tsaya a matsayinki na kanwar matata babu ruwanki da rayuwarmu, kuma ki fice min daga gida yanzu nan” Kamar kyaftawar ido haka ta fice daga falon har lokacin da ta kai gurin motarta bata dauke hannunta daga kan fuskarta ba dan har lokacin bata daina jin zafin marin da yai mata ba. Rahma na shiga dakinta ta dauko makullin motarta da mayafinta ta fito cikin fushi ta fice daga gidan. A gidan Aliyu ya kwana cikin bacin rai, be taba jin zamansa da Rahma ya zame masa matsala ba irin yau, iyakar hakuri zama da ita yana yi iyakar kauna da kulawa yana nuna mata amman bata gani, abu kadan ta shafa mayafi zuwa gidansu bayan ta sani kuma ya sha fada mata ba komai ake fadawa iyaye ba, ba kuma komai ne zaka dauka kace ka tafi gida kai ka yi fushi ba, yawan fushi da kai karar miji yana raba kan in-laws da rashin ganin kimar juna da ganin kamar wani na dannen hakkin wani. Tashi yai zaune yana murmushi ya shafa kansa.Gorin haihuwar da tai masa ne ke bashi dariya daman mace haka take idan ma ita ke daukar dawainiyarka wata rana sai ta goranta maka balle kuma ace lamari ne irin wannan babba. All these years da Aliyu ya dauka na zama tare da Rahma bayan san matsalar daga ita ne ya juyar izuwa ga kansa dan ta samu salama yau shi take gorantawa, sai dai yasan saboda kishi ne komai tai saboda shi ne that's why yake daga mata kafa. Tunawa da zancen roben dazun yasa ya tashi ya sauka kasa ya je gurin data jefarta zoben yana duba har ya hango shi yaje ya dauka yana kallonsa. “Waya bata zobe?” Shine abunda ya fara zuwa masa a rai, Doc Bukar ya fara tunanin sai kuma yake ganin kamar Doc Bukar ba zai yi wannan shirmen ba, ba kawo Muhseen a ransa domin ya san Muhseen ya bar garin nan, bayan su baya tunanin wani kuma sai dai idan a boye yake shi be san da shi ba. Da tunanin wanda ya bata zoben ya kwana a ransa, da kuma tunanin zuwan Rahma gida, shi dai ya daukarwa kansa alkawarin ba zai je bikonta ba domin ba wani abun ya aikata mata da zai sa ta dauki kafa ta tafi gida ba, duk abunda ya fada ya fada nata ne dan ta gyara, beside shi ba son Ataa yake ba to miye abun kishi a ciki after ta san halinsa ba kula mata yake ba ita ma wannan saboda daliline dalilin ma nata. Misalin takwas da rabi na safe ya shirya cikin kananna kaya ya sauko downstairs ya nufo dinning area, rasa yai mi zai a gurin sai kawai ya koma sama ya dauko keys din motarsa ya shiga ya dauki hanyar arkilla. Ataa ce kawai a falon tana gyara Momy kuma tana kitchen, ba karamin dadi ya ji na samun Ataa ita kadai a falon ba, daman yana son ya tambaye wanda ya bata zoben. “Ina kwana” Ta dan risina tana gaishenshi be amsa ba har ya karaso kusa da ita. “Ataa akwai wanda kike so a ranki?” Wani kallo tai masa kamar bata fahimci abunda yake tambayarta ba. “Kina da wani a ranki wanda kike so? Fada min karki baye komai” Kasa tai da kanta tana watsa da kyallen hannunta kamar mai tunani. “Kamal....” Aliyu ya dade yana kallonta kamin ya bude bakinsa ya ce. “Kamal kike so?” Ta yi shiru bata sake cewa komai ba. Sai ya saka hannunsa aljihu ya ciro zoben ya nuna mata. “Shi ya baki wannan zoben?” Sai tai shuru bata ce komai ba. “Ataa ke nan har kin san soyayya?” “Ba son sa na ke soyayya ba, kawai dai ina jindadi idan na tuna dan zaman da muka yi lokacin da muke abuja, ba ya kyamata kuma yana kokarin sakani nishadi” “Lokacin da yai miki wacan siyayyar ne ya siyo miki wannan zoben?” “Ba shi ya ba ni ba” “To waya baki Doc Bukar Ko Muhseen ko wani dabam?” Shiru Ataa tai tana kallonsa kamar wata kurma.“Minene?” Momy ta tambaya tana fitowa daga kitchen ta nufo inda suke. “Je ki kawo min ruwa na sha” Ataa ta nufi kitchen din shi kuma ya matso baya ya zauna saman kujera yana gaishe da Momy. “Lafiya kalau, mi kake tambayarta?” “Jikina na ga tana aiki da safen nan” “Eh nayi na yi ta aje tace tana son ta yu shiyasa na kyaleta” “Okay” Ya fada numfashi na tsinkewa shi dai be jidadin jin wani Kamal a baki Ataa ba domin yana ganin kamar ba soyayya ce abunda ya dace da ita a wannan lokacin ba, bata san ma miye duniya ba amman suna kokarin chusa mata wani abun da be dace da ita ba. Kallonta yake har ta kawo masa ruwan a kofi ta mika masa. “Shaye su ni ba a zuba min ruwa a kofi, je ki dauko min na gora” Momy tace “A a bari ni na dauko maka, ai bata san kan gidan ba” “No Momy ba ri na dauko” Ya tashi ya nufi kitchen din yana jin wani sabon haushin Ataa na lullube shi domin ya fahimci sam bata san kanta ba. ATAA POV. A haka muka tafi be sake tambayata cewar waya ba ni zoben ba, ni kuma ban damu sai na sanar da shi ba, wata kila ma idan ya san gaskiyar Muhseen me ya bani zai rika ganin laifina ne ko kuma wani fadan ya shiga tsakaninsu, domin na lura ko kadan Aliyu baya son ina kula kowa ciki kuwa har da Doc Bukar da nake ganinsa da kima da mutunci, idan ya tarar ina fira da shi ko wata gaisuwar ta hada mu sai ya hade rai ya bata fuska, ko kuma yai ta fushi da ni, ko da yake yanzu fushin nasa ya zame min jiki, ban zan iya fadar laifin da nai masa ba, amman tun daga lokacin da Momy tai masa fadan nan akan matarsa washen garin daya dawo ya tambaye waye ya bani zobe sai na lura da daina sake min kamar da, ni kuma ban damu ba daman ai matar da ta zo min fada ta fada min cewar na shiga hankalina domin be son talaka, daman kuma ni mi zai kai ni sakewa da mutum kamar Aliyu mai ji da kai da ganin kowa na kasa da shi.Satin Nana biyu a asibitim suka sallame ta a tsawon satin biyu da muka yi a asibiti babu ranar da ba ma gaisawa da Muhseen a laptop tun ina tsarguwa har na soma sabawa, a kullum kuma matar sai ta ba ni cake tace daga shi ne. Sau daya ya kawo mana ziyara a asibiti ba tare da sanin kowa ba, domin sai da ya gargade ni akan kar an fadawa Momy cewar ya zo garin nan wai aiki ya zo yi ba zai samu bi ta gidanta ba, ni kuwa a nawa tunanin ya ki sauka a gidanta ne ko yaje saboda Aliyu. Idan na kebe ni kadai bana tunanin komai sai Kamal dan nishadin da muka yi tare da labarin rayuwarsa da ya soma ba ni, tun bayan dana baro gidansu ban sake saka shi a idona ba, hakan kuma ba karamin haddasa min damuwa yai ba, ko yana ina yanzu? A wane hali yake oho? Wata kila ma ya manta da wata yarinya mai irin sunana. Daddy Siyama sau uku ya zo ganin Nana yana da son mutane sosai ya nuna mana kulawa har ya dauki kudi ya bawa Nana bayan irin dimar da Momy take da mu. Ranar da aka sallamo Nana asibiti da kafafunwanta take tafiya, Momy na tare da ita yayinda ni da Siyama muka yi gaba muna tafiya, motar Amina muka shiga ni da yan uwanta Momy da Nana kuma suka shiga motar Aliyu. Na yi zaton Clapperto road zasu nufa da mu domin sauke mu acan sai na ga an nufo gidan Momy da mu. Aliyu ne ya budewa Nana mota da kansa ta fito tana takawa a hankali tana bin bayan Momy wacce ta wuce gaba zuwa cikin falon. Ina lura da yadda Nana take karewa ko'ina gidan kallon, wata kila ita ma ya burge ta kamar yadda ni ma burge ni a farkon zuwana. A falon muka zauna Momy na ta murmushi ta ce “To Nana kin ga gidanmu idan kin dan huta za ku koma bq na saka an gyara muku can za ku zauna ke da Ataa, kuma dan wajen Fulani yace zai nema mata makaranta nan kusa sai ta fara zuwa islamiya, ta bokon ma za a samu wanda zai fara koya mata a gida kamin a saka ta makaranta” Ban san lokacin da idona ya cika da kwalla ba, na dade ina jiran zuwan wannan ranar da zan koma makaranta na samu ilimi, amman ban samu ba. Kallon Aliyu nai sai naga yanayi ma Nana murmushinsa kadan muna hada ido ya murtuke fuska kamar be taba dariya ba wai kar na ga damarsa.“Na gode” Na fada murya kasa kasa. Be amsa ni ba sai ma dauke kansa da yai daga barin kallona ya kalli wani gurin dabam. “Kana ta hidima da mu, bayan nema mana magani yanzu kuma kun kawo mu a muhallinku, kuma za ku nema wa Ataa karatu? Abunda na dade ina mata burin samu amman na kasa bata, ban tana haduwa da mutane masu karamanci da sanin darajar dan 'adam ba irinku, taimakon da kuke mana ya yi yawa da me za mu saka muku?” Cewar Nana tana hawaye kamar yadda nima na ke yi. Momy ta yi murmushi “Ba komai ai yi ma kaine, lokacin sakarwa zai zo lokacin da zan nemi wani abun daga gareki ina fatar ki amsa min da hannu biyu” “Zan karba miki ko mienene a duniyar nan, matukar ina da iko da karfi akansa, ku ne mutanen da kuka mai mu mutum, ban tana mafarki haduwa da ku ba, kuma ba ku taimake ni dan ku samu wani abun daga gareni ba” Har yanzu Nana hawaye take hawayen jindadi da farinciki. A nan muka ci abinci suka koshi sannan Amina ta raka mu zuwa bq din, wani bangare ne na gidan da aka kawata fulawoyi sam ba zaka dauka cewar bq bane sai idan an fada maka, dan madaidacin daki ne mai bandaki a ciki, haka aka jera dakunan har biyar kowa ne da bandaki a ciki, sai dai na mu shi aka sakawa katifa ta labule da zanen gado aka gyara ko'ina tas kamar ba bq ba. ALIYU POV. After Nana ta huta, Amina ta nuna musu bq ita da Ataa. Sai ya rage falon daga shi sai Momy. “Momy Rahma bata gida har yanzu” Kallon mamaki Momy tai masa. “Ban gane ba?” “Tun wacan lokacin da muka samu misunderstanding akan matsalar Ataa shikenan tai fushi ta tafi gida” “Kana nufi duk tsawon lokacin nan bata gidanka?” “Tana gidansu” “Kuma iyayenta ba su kira sun bincike matsalar ta ba?” “Da za su kira ai da sun kira ko kuma Abbah ta ya kira Daddy ya ji ko mienene matsalar” “Hmmm Allah ya kyauta, abunda suke yi ma yarinyar suna ganin kamar so ne ko gata Wallahi suna lalata mata rayuwa ne kawai, abun kadan yarinya tace ta tafi gidansu sai kace wata mai shan nono” “Ni dai Momy so na ke a shirya mu da ita na yi alkawarin ba zan je bikonta da kaina ba domin ni ne mai gaskiya” “Ai da ka bi ta tawa ka barta can gidansu ta dandana zaman gidan ta ji idan da dadi kamar na gidan miji, kishi hauka ne ko cewa kai tana son Ataa laifi ne balle baka furta ba, haka ake rayuwa” “Momy ni dai ayi hakuri a dawo min da matata dan Allah” “Na ji sai Daddyn ka ya dawo ai ko?” “Tau na gode” Ya fada, ba dan komai yake son a dawo masa da Rahma ba, sai dan yasan ita kanta tana cikin damuwarsa a yanzu duk kuma abunda ta aikata saboda shi ne, domin tana son sa tana kishinsa ne, after that yana son matarsa a kusa da shi shi kanshi ya san yayi hakuri iya hakuri har na sati biyu ba tare da Rahma a kusa da shi ba, hakan na matukar damunsa domin ya san ita kadai ce a duniyar ke iya yaye masa wannan kishin da yake ji matukar ba alfasha zai aikata ba. Husna ce ta fito manne da waya a kunne tana tambayar Momy ina Ataa. “Wake nemanta?” “Ya Muhseen ne ya ce a akai mata waya” “Tana bq” Momy ta bata amsa sai ta nufi hanyar fita daga falon, Aliyu ya bita da wani kallo kamar ita ce Ataa. ZAKI By Khadeeja Candy 37... “Momy idan ba ki takawa Muhseen burki tun yanzu ba, zai iya wuce guri fa” Momy ta masa kallon rashin fashimta. “Wuce guri kamar ya?” “For god sake Momy taya zai rika nunawa yarinyar wata soyayya a yanzu? Allah kadai yasan irin kalaman da ya ke furta mata” “Shi kiranta a waya har wani nuna soyayyah ne? Idan ma haka din ne ai sonta yake sai ya fara nuna mata yana sonta? Dan wajen Fulani ka rika kyautatawa Muhseen zato, ka fi kowa sanin cewar ba mugun mutum ba ne kuma ba dan iska ba ne” “Na sani, amman ke kanki Momy kin san Mama Fulani ba zata bari Muhseen ya auri Ataa ba saboda tana ganin darajar Ataa da ita ba daya ba, shi kansa ya sani kawai yana son ya batawa yar mutane lokaci da rayuwa ne kawai, daga lokacin da ya samu damar kaiwa ga jikinta Wallahi ba zai sake cewa yana sonta ba, domin kyauta yake gani, kyaun da idan ya samu dama zai iya zaga mata rigar mutunci shikenan kuma ta daina burge shi, idan ba a taka masa burgi yanzu ba nan gaba karatun da ake son ta yi ma kasawa za ta yi domin soyayya kawai zata sakawa gaba” Murmushi Momy tai tana ma danta wani kallon na fahimtar wani abun da shi Aliyu be san da shi ba. “Idan ma haka ne, ai sai ta aureshi ta cigaba da karatunta a gidansa ja ga babu wani zancen daukar hankali, kai ka kanka mai nemawa Muhseen aurene fa, balle kuma ni da na ke uwarsa, hankali dai ya kwanta kawai”Mikewa Aliyu yai tsaye domin maganar Momy sam bata masa dadi ba, dinning ya nufa ya zauna ya zubawa kansa abincin rana da be samu ci ba ya maida hankalinsa yana ci ba dan abincin yana masa dadi ha duk kuwa da kasancewar abunda yake so ne aka girka, ba kuma zai iya fadar dalilin rashin jindadin abincin ba, ci yake hankalinsa na can gurin Ataa wacce Husna ta kai mata waya, kamin ta dawo duk ya takura, ji yai ba zai iya hakura ba ya tashi ya fice daga falon gaba daya zuwa bq, a gurin aje motoci ya samu Husna tsaye tana jiran Ataa dake can gefen fulawoyi ta gama wayar ta bata wayarta. “Ke kar Muhseen ya sake kiran wayarki ya ce ki bawa Ataa ki kai mata, na hana daga yau” “To ba zan sake ba” Ta amsa da sauri tana gyada masa kai. Ya nufi inda Ataa take zaune wayar a kunnenta tana murmushi hannu kawai ya mika mata alamar ta bashi wayar, sai ta tsaya kallonsa ba dan ba ta fahimce shi ba sai dan jira take sai ya furta. “Wani wayar” Ya furta da karfi sai ta mika masa tana kallonsa da fararen idanuwanta masu kamar madara ta turo masa baki alamar ta ji haushi, katse kiran yai sannan ya nuna ta da wayar. “Karki sake waya da Muhseen a cikin gidan nan” Bata ce masa komai ba bayan idon da ta sakar masa shi kuma ya juya ya koma gurin Husna ya mika mata wayarta sannan ya bude motarsa ya shiga ya bar gidan. Duk abunda suke Momy na hangensu ta windows din kitchen murmushi tai tana ta kallon yadda Ataa ta turo baki, ta sani da ace wata ce a cikin kanensa wata ta turo masa baki yau sai ya fasa bakin nan amman da yake Ataa ce gashi ya tafi ya kyaleta, yadda Aliyu yake nuna kishinsa akan Ataa ta sani sarai son Ataa yake ba wai yana gudun shigarta wani halin ne kawai ba, sai dai shi din be san yana yi ba. Shigowar Husna a kitchen din yasa Momy barin jikin windows ta kalleta still tana murmushi. “Momy kin ga Ya Aliyu da fusata wai kar na sake bawa Muhseen wayata su yi waya da Ataa, gashi Yanzu Ya Muhseen din kiran ma yake na ki dagawa ban san mi zan ce masa ba” “Ina hangenku ai, idan ya sake kira kice ni ya kira a wayata zan bata su yi wayar” “Okay tau” Husna ta juya ta fice daga kitchen din, Momy ta dafa kitchen cabinets tana fadin. “Lokaci da yana zuwa, zancena zai tabbata wata rana, zaka duka har kasa kana rokon yar talakawa ta so ka lokacin da ba zan iya maka komai ba, domin ba zan zabe ka na bar Muhseen ba ko kuwa ina son hakan, amman ko ba komai son yarinyar nan zai maida kai namiji na jidadin da kake kishi a yanzu, at least zata koya maka kishin matarka, zaka fahimce wayewar zamani da boko ba komai ba ce idan aka hada ta da addini”Ita kadai take magana da kanta cikin yanayin na rashin jindadi. Ba ta bar kitchen din ba sa da ta dora girki dare. Yau Daddy dawowar maraice yai domin ana daf da kiran sallah magariba ya shigo gidan, direbansa ne ya bude masa mota sannan ya fito ya dauki jakarsa ya shigar masa da ita part dinsa, Daddy kuma ya nufo part din Momy yana gyara zaman babbar rigarsa, tun kan ya kai hannu ya bude kofar ta bude masa fuskarsa da murmushi. “Sannu da zuwa” “Yauwa” Ya amsa yana naso kafarsa cikin falon, kujerar da ke kusa da kofa ya zauna yana sauke agajiya, Momy ta nufi gurin freezer dake gefen dinning ta dauko masa gorar ruwa da kofi ta kawo masa. “Yau dawowar wuri akai SSG?” “To mun gama abunda za ayi, zama na me kuma?” “Ai ko ka dawo a daidai, da na so ma na kira kuma ban samu dama ba” Sai da ya sha ruwan da ta mika masa sannan ya kalleta ya ce. “Wani abun ne?” “Dazun ne Dan wajen Fulani yake fada min cewar wai Rahma bata gidansa tun sati biyu da suka wuce” Daddy yayi fuska manya irin ta mamaki da son tantace magana. “Tana ina?” “Wai ta yi fushi” “Fushi? Fada suka yi?” “Ba fada suka yi ba, kawai dai akasan yarinyar nan da ke jinya asibiti, ita Rahma ta saka aka je aka daketa da zo na fada masa shi ne tai fushi” Daddy ya kyalkyale dariya kamar ba wanin abun ba. “To ko kishi take? Yaushe akai abun?” “Tun sati biyu da suka wuce dazun ma aka sallamo Nana daga asibitin, ni ban ma sani ba sai dazun yake fada min wai a masa bikon matarsa” “Kuma fa muna yawan haduwa da Alhaji Nasiru Gobir be taba min maganar ba” “Wata kila yana maka kallon ka sani ne” “To Allah kyauta mutanen ne basa da dattako sam, ace yarka ta dawo gida har na tsawon sati biyu ai ya kamata ya bincika ya ji miye dalili” “Dalili ya wuce bin bayan yarsa, kasan duk abunda ta fada shine daidai, sam ba su mata tarbiya mai kyau ba, ace abun kadan ka debi kafafuwa zuwa gidanku, yarinya lafiya ma bata isheta ba duk dawainiyar da yake da ita basa gani, wani lokacin Wallahi har tausayi yake bani, kwata kwata dan wajen Fulani ba san dadin aure ba” “To shi kuma a haka son abarsa yake, da dai ya samu wata ya kara ai ita ma zata bawa kanta lafiya, mace idan tana ita kadai kuma tana ganin gata ya mata yawa zata ta yi abubuwa da dama ai, ko da yake Aliyu dan boko ne ba son mata biyu yake ba” “Ba wani gata rashin tarbiya dai ne tun a gida ba a koya musu tarbiya mai kyau ba, ni da gatan be saka na yi wani abun ba” Daddy ya mike tsaye yana zolayar Momy “To ke duk kika gwada yi ai sai a kawo miki kanwa, ga mata nan duk inda na shiga kallo na kawai suke” Momy ta dan harare shi. “Ai ba kai suke kallo ba mukamin ka da kudinka suke kallo, idan ba dan kudi ba waye zai so tsoho? Ko ma watan ka kawo ai na gama cin moriyarka kuma na zama uwargida mai yayan gida sai dai ta bi” Dariya suka yi har ita da tai maganar domin ta kareshi maganar ne tana wani murmuda ido irin na su na manyan mata. “Ina yarana? Ban ji motsinsu ba” “Husna da Amina sun fita Siyama kuma tana can bangarensu Ataa” “To Alhajin Fulani ya samu cigaba kamfanin nan da yake ikirarin za a siyar wani dan kasuwar kasar nijar ya siye shi, Kuma ya bar ragamar tafiyar da kamfanin a hannunsa, ya kamata ko ban samu zuwa ba ki shirya da yara ko kwana daya ne suke ku masa murna, samun cigaban dan'uwana kamar nawa ne, ba ni da wani wanda ya fi shi a yanzu” “Gaskiya na masa murna sosai, Allah ya dafa ya taimaka, daman haka muke so ai, to wannan tafiyar fa?” “Ki samu wata kuje daman biko ai na mata ne” Yana fadar hakan ya fice daga falon ta biyo bayanshi tana ta taya shi murnar samun siyen kamfanin da akai har tana fadar ranar da ya dace suje.Bayan sallah magariba Momy ta kira kawarta Hajiya Ramatu ta fada mata cewar za su je bikon Rahma. After sallah isha'i idan tana da time, ana saukowa daga sallah isha'i sai ga Hajiya Ramatu ta zo gidan ita da danta wanda shi ya janyo motar ya kawo da ita a gidan, tana shiga falon Momy ta fito sanye da mayafi suka gaisa a tsaitsaye suka koma cikin motar Hajiya Ramatu, kamin su isa gidan Alhaji Nasiru Gobir wato mahaifin Rahma Momy take labartawa aminiyarta Hajiya Ramatu abunda ya faru tsakanin Rahma Aliyu. Tsaki Hajiya Ramatu taja cike da jin haushi ta ce “Wai Hajiya Hadiza miyasa ba za ki saka Aliyu ya kara auren ba? Wannan iskacin da jin kan da yarinyar nan take masa ya yi yawa, wallahi idan yanzu ya kara aure duk wannan iskancin dainawa za ta yi kuma dole ta kama kanta idan ta ji ba zata iya zama ba ta fita” “Kamar a gaban ki akai, Wallahi dazun mahaifinsa ma haka yace kin san ko maza ma basu cika kula da sha'anin aure kamar mu mata ba” “Wallahi akwai haushi Hajiya Hadiza abunda ake masa ne ai yayi yawa, duk irin hidimar da yake musu basa gani? Bawa ne shi?” “Ido ne nawa idan ya ji wuya shi zai nemi karin auren da kansa ai, amman na san da Fulani ta san da wannan Wallahi da sai tana zuwa bikon nan daman can ba son aurenta da Rahma take ba” “Ke ma dai ai da ba ki je ba Wallahi da ya zuba musu ido ya barta tai ta zaman gidan har sai zaman gidan ya isheta” “Kin san iyayen miji idan ba su yi ba, basa fita idan ma suka kai ba fitar suke ba, yanzu ma sai an dora laifin a kanmu” Hajiya Ramatu ta tabe baki cike da jin haushi. Ba laifi yan'uwan Rahma yayanta da kannen sun tarbesu cikin girmamawa da mutunci, sai dai mahaifiyar Rahma na fitowa sai ta canja musu fuska kamar wacce bata son zuwansu. Ciki ciki ta gaisa da su Momy na ganin hakan ta dauke kai ta ki cewa komai sai Hajiya Ramatu ce tai bayanin abunda ke tafe da su. “To ya gaji kenan? Yarinya ta zo gidansu sati biyu dan tsabar wulakanci be zo ba be aiko ba, sai yanzu idan ya gaji da ita ai ba sai ya wulakanta akan yar talakawa ba, wai har ya mari Muneera akan wata banza can sha sha sha, yarinyar da be san inda ta fito ba, idan ma gajiya yai da ita mu ai muna son ta ba mu gaji da ita ba” Wani wawan kallo Momy tai mata har tana kashe ido tsabar bacin rai. “Yar talakawa da ba a san inda ta fito aka dauki kodarta aka sakawa yarki, sai yanzu na gane ashe Rahma bata rage komai daga halinki ba, ke kika koya mata kyamar talaka talakar ma wacce ta taimake ke ku, ba mu damar zuwa bikon Rahma ba sai yanzu, shi kan shi mijin na ta ma be so mun zo ba, domin ba shi ya koreta daga gidan ba, yarinya kamar wata mai shan nono da an yi abu ta dauki kafa zuwa gida ko kunya babu, mi Rahma zata nuna mana? Gata ko kudi ko family? Ba ta nuna mata dukiya ke kanki kin sani zuri'a kuma duk sokoto an sani babu wanda ya fi torankawa asali da tarin yan'uwa, duk abunda take muke shanyewa muna shanyewa ne saboda muna son ta zauna lafiya da mijinta, domim Rahma bata san wani abu wai aure ba, dan abu kadan ta kwaso kafa zuwa gida haka ake yi?” “Au daman ba shi ya aiko ku ba kuka zo? To ki koma Rahma ba zata koma yanzu ba sai ta huta, sai Aliyu tako da kansa ya dauki matarsa, dacan idan ba nan ba so kike ta koma gefen titi tana bara kamar yar da danki ke so? Abun kunya wai kamar SSG ace dansa yana son yar bara a titi, mutum mai daraja wanda ya rika mukamai masu girma ace an rasa wacce dansa mai kamfanin Sky global resources yar talakawa makaskanciya, ku kanku ai abun kunya ne a wajenku”Momy ta girgiza kai tana kiran sunan Aliyu baro baro. “Sam ni nikam abun alfahari ne yau Aliyu ya auri Ataa ko babu komai zai inganta rayuwarta kuma sai san yayi aure, ya kuma gane banbancin tarbiya da rashinta” “Daman ai saboda kin cusa nasa son wata ne kike wannan bobotan, indai yana son Rahma ta koma dakinta to ya janye neman aurensa da wannan kazamar yarinya, ya hada Rahma kishi da yar wani mai kudi ba amman ba wannan ba” Momy ta yi yar dariyar takaici tana mikewa tsaye tare da Hajiya Ramatu wacce ta kasa cewa komai tun da aka fara fada. “Hajiya Talatu kin yi tutu gonar mai munta, zaman gida dai ko? Rahma tai ta zama har Mahdi ya bayyana, idan kuma zaman ya isheta sai ki dauke ta ki kaita dakinta, amman wani daga ni ko Aliyu ba zai zo bikon wannan yar ta ki ba, kuma ki zuba ido indai ina raye Rahma sai ta kishi da yar talaka...!” Momy na kawai nan ta nufi kofar fita a fusace, daf da zata fice Hajiya Talatu Mommyn Rahma ta ce. “Ai dole ku nema masa yar talaka, domin kin san babu yar gata gabas da yamma da zata zauna da juya, dimmar da yai mata ai ya mata ne saboda ya san baya haihuwa su taru su mutu tare” Momy ta juyo ta kalleta. “Ke Hajiya Talatu idan ba ki gode ni'imar Allah ba za ki gode ma azabarsa, ruwan cikin lokali ya ishe mai hankali wanka kuma ki rubuta ki aje da ikon Allah sai Aliyu ya yi aure ya haihu....” A fice Momy ta fice daga falon tana nadamar zuwan bikon da tai. Momy na fita Rahma ta fito idonta shakaf da hawaye ta fadi a kusa da Mommynta kamar zata narke. “Na shiga uku Mommy mi yasa kikai fada da su? Na rantse da Allah Aliyu ba zai zo bikona ba, tun da kika taba masa uwa, Wallahi ba zai sake ganin kimata ba, Aliyu baya son a taba masa family” “To sai mi? Aliyu shi kadai ya rage a duniya ne? Ko sakin ki yai sai kije ki auri mai haihuwa ki haihu, kar wannan abun ya daga miki hankali matukar yana son ki dole ya dawo, ai yasan gidan da ya dauke ki gidane mai daraja da kima” Cikin kuka Rahma ta tashi ta koma dakinta, Muneera ta taso daga dayan bangaren na falon daman falon ya kasu biyu ne, ta nufo inda Mommynsu take tana dariya.Husna ta tashi ta nufi karamin firjin din dake dakin ta dauko mata ruwa da kofi ta kawo mata ta zuba mata, sai da Momy ta sha sannan ta labartawa Husna abunda ya faru. “Mutanen nan suna ba ni mamaki, wai talauci hauka ne? Shikenan dan suna da arziki sai su taka mutane yadda suka ga dama” “Su taka wanda yake neman abu gurinsu dai, arzikin da ba na shi ba, mai tinkaho da abun wani duk uwar dukiyar da yake kuri da ita idan aka kasa uku ko kashi daya ba zai dauka ba, dukiyar wani ce wanda idan yau ya kaushe abarsa sai dai tu koma rabe raben wani, shi har abun tinkaho ne? Wai wanda ya gaji arziki baya haka” “Gaskiya abunda suke yayi yawa, haba jama'a wai Wallahi sun ja mata domin Ya Aliyu ba zai je bikon ta ba” “Tai ta zama a can har sai zaman gidan ya isheta ta yi hankali aure dai sai Aliyu yayi kuma Ataa zai aura sai dai su mutu?” “Momy da Ataa?” Husna ta tambaya tana zare ido. “Eh ba ni za su nuna isa ba? Sai ya aureta?” “Ya Muhseen fa?” “Amina zan bashi, daman ai Fulani ba zata yarda ya aureta ba, kuma ko aurenta yai ba dadin zaman zata ji ba, amman yanzu Aliyu nake son ya aureta ya maida mutum kamar yarsu in ya so sa su mutu” “Amman Ya Aliyu zai yarda ya aureta ne? Kin san fa ba sonta yake ba?” “Ba son ta yake ba yake kishinta? A banza ake kishin mace? Idan ma baya son ta sai ya fara daga yanzu” Cewar Momy tana wani cika har yanzu zuciyarta ta ki ta sauka daga bacin ran dake tare da ita. “Amman Momy Ya Muhseen zai ga kin masa rashin adalci” “Na ce miki Amina zan ba shi ai yasan idan bana sonsa ba zan ba shi yar cikina ba, amman Ataa sai ta auri Aliyu In-Sha-Allahu” “Idan kuma ita Ataa din bata son shi fa?” Momy ta yi shiru alamar tunani kamin ta daki kan gadonta tana ta rawa da kafa. “Ina bukatar sanin waye Ataa ina suka fito, shine kawai abunda na ke son sani a yanzu, amman bayan shi talauci ko wani abun ba zai hana wannan auren ba” Husna dai ta kalli Momy ta janye fuskarta tana tunanin yadda za ayi wannan chakwakiya domin Muhseen ma ba kyalle ba ne, kuma yadda yake nuna yana son Ataa yana da wahala ya iya yarda ta auri Aliyu yana kallo. Haka Momy ta kwana da bacin ran abunda ya faru ta tashi da shi, Daddy kan dariya kawai yake mata daman haka yake mata idan ta saka kanta a wani abun at the end kuma be yi kyau ba, sai dai bata fadawa Daddy kudirin na na aurawa Ataa Aliyu ba, domin ta san ba zai zabi Aliyu ya bar Muhseen ba, duk kuwa da kasancewar be san Muhseen na son Ataa ba, bayan maganar tafiya Abuja da suka aje jibi babu wata maganada ta sake masa.Lokacin data dawo part dinta bakwai da kwata ne na safe, sai da ta fara shiga kitchen ta kunna gas ta dora ruwan zafi sannan ya fito falon tana dauke da dankalin turawa ta shiga dakin Siyama, sai ta same ta zaune tana home work din da bata samu yi jiya da dare ba. “Momy ina kwana?” “Lafiya kalau rubutu kike?” “Eh homework ne da ban yi ba jiya” “Okay ba ri na kaiwa Husna ta gyara min dankalin” Ta fada tana juyawa ta fice daga dakin Siyama zuwa na Husna, ita ma zaune ta sameta sai dai waya take tabawa, tana ganin Momy tai saurin saukowa daga saman gadon da kayan bachinta ta karbi robar hannun Momy. “Momy ina kwana?” “Lafiya kalau kin tashi lafiya” “Lafiya kalau? Ya bacin rai?” “Ba zai gushe ba ai sai na cika burina, kar wannan maganar ta fita ki barta tsakanina da ke ko Amina bana son ta ji” “In-Sha-Allah Momy” “Idan kin gyara dankalin ki kawo kin kitchen, kuma kin san bana son kazanta ki fito waje ki gyara ba a daki ba” Momy ta juya ta fice daga dakin Husna, da kanta ta shiga dakin Amina ta taso daga guntun bachin data fara na safe. “Amina ta so muje kitchen ki min wanke wanke” “Tau” Ta fada tana sauko daga kan gadon sanye da doruwar rigarta, Momy na gaba Amina na baya har suka shiga kitchen din, sai da ta soma hada kayan wanke wanke ta tana wankewa Momy kuma na shirya abun karin kumallo ta ce mata. “Amina Muhseen fa ta fadawa Daddy ku wai a tambaya masa ke idan kina son sa?”Amina ta ji abun wani banbaragwai. ta tambaya har tana nuna kanta “Ni...?” “Ke fa” “Ya Muhseen ba Ataa yake so ba?” “Nima haka nai zato, yace idan zan je yi ma Abbahsu murna na wuce masa da sako” “Yaushe za ki je?” “Jibi shiyasa na ke son jin ta bakinki tun yanzu, idan ma tunani da shawara za ki yi sai ki yi kamin na tashi” Dariya Amina tai domin sam bata dauka da gaske Momy take ba. “So dai suke ku hada mu Momy, amman Ya Muhseen ai Ataa yake so” “Karya zan miki kenan?” Amina bata sake cewa komai ba bayan dariyar da tai. ATAA POV. Da wani kallon haushi na bi Aliyu bans an dalilin son nuna isa da yake min ba, abunda yake min ko kanensa baya yana ma haka, domin su ai suna wayar be taba hana su ba sai ni. Haka na tashu ta tunzure bakina na tafi bq din mu na zauna bakin kofar dakin da Nana take ciki kwance, ina ta jin haushin karbe wayar da Aliyu yai domin ban gama waya da Muhseen ba, kuma ina son idan mun kai karshe na tambaye ko yana da labarin Kamal amman wannan bakin Aliyu ya zo ya karbe wayar. Bayan sallah isha'i Siyama ta kawo mana abinci a wata kula da plates mai kyau, tuwon shimkafa ne da niyar ganye ban wani ci sosai ba amman Nana ta ci shi sosai har sai da ta rasa masokar tsintsiya a cikinta. A katifa daya muka kwanta, kasancewar yarwantacciyar katifa ce ba kamar gadon asibiti ba da iya mutum daya yake dauka, katifar mai fadi ce sosai amman na matse bayan Nana na kwanta jikinta kamar zan tsaga bayanta na shige ciki, nai bachina cikin kwanciyar hankali har safe. Bayan mun gama sallah Nana ta ce shiga bangaren Momy na taya ta aiki, ni kuma ban shiga ba sai da rana ta fito domin a tunani ba su farka ba a wannan lokacin duk kuwa da na san suna tashi sallah asuba amman ai suna komawa. Har na fita haka sai kuma na dawo na dauki Hijab na saka gudun kar na hadu da Aliyu ya sake min masifar ban saka Hijab ba, ko da na shiga part din a samu Momy a kitchen Amina kuma tana zaune falo rike da remote tana kallon tv sai dai kana ganinta kasan hankalinta ba a gurin tv yake ba. Sai da na gaishe ta sai na sannan na nufi kitchen din dan gaishe da Momy sai na same ta tana waya, da alama da Mama Fulani take wayar domin na lura tana cikin far'a har ma tana fadin jibi za mu zo, sai da ta gaka wayar ta sauke sannan na gaishe ta amsa, na nufi inda kofar bayan kitchen din take dan dauko tsintsiya na ce. “Momy Abuja za ki je?” “Eh jibi In-Sha-Allah ko za ki je?” “Eh Momy” “To ki shirya da wuri yata” “To na gode” Wani irin dadi ne ya lullube ni, babu wanda na kawo a rai na sai Kamal, zan jure wulakanci Mama Fulani tun da da Momy za mu je kuma saboda Kamal zan je, haka na share gidan tsaf cikin nishadi, a dayan bangaren kuma ina tsoron kar Aliyu ya zo ya hana ko kuma ya iya zama tafiyar mai dadewa cewa ba zai yi naje na bar Nana ba, sai idan tafiyar kwana biyu ce. **ZAKI By Khadeeja Candy 38... Juyi yake ta yi akan gadon idonsa biyu ba dan yana jin bachi ba sai dan kishin da ke tare da shi, lips din bakinsa ya ke cizo kamin ya unkura ya tashi zaune yana shafa kansa. Short and white ves ne a jikinsa ya samu minti goma a haka sannan ya mike tsaye ya ware red curtains din dakin, ya bude class windows din haske ya shigo sai ya juya yana kallon bed dinsa. Sai kuma ya nufi kofar fita daga bedroom din, kasa ya sauko kai tsaye ya nufi kitchen ya kunna electric kettle ya dauko wani kofin ya matsa lemun tsaki da kanwa a ciki, ruwan zafin na tafasa ya zuba a cikin kofi ya bar shi a haka ya dauki wani kofin ya hada Lipton da suga kadan, sai da ya jira lemun tsamin da kamwar sun dan huce sannan ya dauka ya sha ya dora da ruwan Lipton din. Freezer ya bude ya dauko kankara a gorar ruwan faro ya dawo bedroom dinsa ya shiga bathroom ya fashe kankanrar ya zuba a cikin bokiti ya sirka da wasu ruwan ma su dan dumi yai wankan da ruwa mai sanyi sosai sannan ya fito daure da tawul yana jin ya samu relief. Be dauki minti talatin ba tsakanin shafa mai da saka tufafinsa wani irin kuzari yake ji sosai, kamar ba shi ne ya kwana a gado jiya kamar marar lafiya ba. Maroon shirt ya saka da white jean colar shirt din ta karbi jikinsa sosai ta kara fito da farinsa da kuma kyan fuskarsa, haka ya firo harabar gidan fuskarsa har ya wani annuri take. Tun kan ya karasa gurin motar ya danna keys din hannunaa yai kara hakan ya hankaltar da mai gadinsa yai saurin isa gate ya bude masa tun kan ya tashi motar. Yana shiga yai mata key ya dauki hanyar arkilla wato gidan Momy, daman ba shi da gidan zuwa sai can ko lokacin da Rahma take nan balle yanzu da bata nan. Sau daya ya danna horn mai gadin ya bude masa gate, kusa da inda Ataa take zaune tana gyaran doya ya faka motarsa, zaunawarsa yai a motar yana ta kallonta ta cikin gilashin motar, ita ma kallon bakin gilashin motar take ba dan ta san wanda ke ciki ba, sai dan yau murna take Momy tace zata je da ita Abuja, murmushi kawai take abinta kana ganinta kasan tana cikin farinciki sosai. Ya dade yana ta kallonta kallonta na burge musamman idan shi kadai yake kallon nata ba tare da ita din tana kallonsa ba, domin yana tsarguwa idan tana kallonsa. Samun kansa yai da murmushi ganin murmushi a fuskarta duk kuwa da be san silar farincikin nata ba, but seriously ta burge shi and he like her smile more than everything yanzu, bude motar yai ya fito har ya rufe ita yake kallo ita kuma sai murmushi take mishi har da wani. “Laaa kai ne? Ina kwana?” Be amsa ta ba ya nufi bq yana ta mamakin dalilin farincikin nata ko mi akai mata take wannan far'a oho. Ko davya shiga Bq Nana na zaune balcony tana kallon itacen guava dake kusa da bq din, har kasa Aliyu ya risina ya gaishe da ita yana wani kasa da kai kamar mai jin kunya. “Ina kwana?” “Lafiya Kalau, ke tashi lafiya?” “Lafiya kalau ya jikin na ki” “Al-hamdulillah, Allah ya saka da alheri mun gode mun gode sosai” “Ba komai, idan dai kina bukatar wani abun ko kuma kinji wani abun sai ki yi magana” “Yayi kyau ba matsala In-Sha-Allah, Allah ya biya” Ta fada da murmushi a fuskarta har ga Allah Aliyu yana burgeta yadda yake hidima da ita da kuma irin kulawar da yake nuna mata tana jindadi sosai, wani karin abun farinciki ma da Ataa ta fada mata har jininsa ya bada aka saka mata sai ta ji kamar ta dauki zane ta goya shi a bayanta.Ya fito bq din yana wasa da bq din hannunsa yana murmushi, at least now na durkusa har kasa ya gaishe da Nana bayan gaisuwar da ya taba mata a asibiti da risinawa, abun ya burgeshi shi kanshi ya ji kanshi a wani mutum daban. Murmushi da Ataa ta gani a fuskarsa lokacin da ya fito bq ne yasa ta kyalkyale da dariya for no reason tana kallonsa, kallonta yai har sai zai wuce ya shiga falon Momy sai kuma ya ji ba zai iya ba sai ya ji dalilin wannan farincikin da Ataa take yi. Karasowa yai kusa da ita ya tsaya a akanta ita kuma ya daga kanta sama tana kallon still murmushi a fuskarta. “Mi akai miki kike dariya?” “Ba komai” “Ba koma kike jindadi?” “Momy ce ta ce zata je da ni Abuja, kwana biyu zata yi ta dawo” Yasan Mama Fulani bata son Ataa kuma ta yi ta gana mata zaba ita da yayanta, dan haka ataa ba dadin zaman dake ji a can ba, to miye abun murna dan ance za a kai ka inda ba dadi kake ji ba. “Miye abun murna a cikin?” “Idan na je ai zan ga Kamal ko?” Ta fada da sigar tambaya kamin ta cigaba. “Shine na ke jindadi ai” Ta fada tana murmushi ba tare da ta bude hakoranta ba, wani irin abu ya ji ya daki kansa ya soki zuciyarsa yayi cikin ɓargonsa, a take ya nemi nishadin zuciyarsa da na fuskarsa ya rasa, ya wani hade rai har idonsa na canja kala. “Ita kuma Nana ki bar ta a hannun wa?” Ta yi shiru tana bata fuska sai ta soma yanka doyar da karfi tana jin haushin maganar da Aliyu yai a yanzu. Be sake ce mata komai ba ya nufi kofar falon ya tura ya shiga, Amina ce har yanzu zaune a falon remote a hannunta kamar dazun Husna kuma na kitchen ita da Momy. “Ina kwana Yaya?” “Lafiya Kalau” Ya amsa mata kamar baya son karbawa. Tashi tai ta nufi dakinta shi kuma ya nufi kitchen. “Ina kwana Ya Aliyu” A takaice ya amsawa Husna yana mikawa Momy nata gaisuwar. “Lafiya, Momy ina kwana?” “Lafiya kalau, Husna ki hada da doya idan Ataa ta kawo” “Okay” Husna ta fada tana cigaba da soyan dankalin da take Momy kuma ta juyo ta fito daga kitchen din zuwa falo tare da Aliyu, yana ganin yanayin fuskarta ya sam bata cikin nishadi, sai da ta fara zaka sannan shi ma ya zauna. “Momy ke kika ce zaki tafi da Ataa Abuja?” “Waya fada maka?” “Ita ta fada min yanzu” Momy ta yi murmushi. “Eh Daddynku ya ce Abbah ya samu mai siyen kamfanin nan an har siye kuma an biya kudi za a cigaba da komai karkashinsa, ni ban ma sani ba sai jiya shine yake cewa ya kamata muje mu masa murna ko da shi be samu zuwa ba, to ta shigo ta tarar ina waya da Fulani ta ji zancen zuwa Abuja shine ta ce tana son za ta bi ni” “Karki je da ita Momy” “Saboda me?” “Mahaifiyarta wa za ta barwa ita? Kuma ko tafiya kika yi da ita Muhseen daukarta kawai zai yi yayi ta yawo da ita” “Wannan ai ba hujja ba ce, daga ni sai Husna zan je sai kuma ita, Amina da Siyama ai za su iya kula da Nana, tun da zata iya kai kanka bandaki ta fito da kanka” “Momy karki je da ita dan Allah, Wallahi saboda ta ga Kamal zata je, yarinyar nan tana son sakawa kanta soyayya da kurciyarta, Wallahi idan ba a takawa yarinyar nan burki ba zata iya lalacewa” Momy ta yi dariya. “Ita tace maka saboda Kamal zata je? Son Kamal din take ne?” Yayi shiru be ce komai ba ganin Ataa ta shigo dauke da robar doyar da wuka. “Gashi Momy” “Kai kitchen” Kai tsaye ta nufi kitchen din, Aliyu ya kalli Momy ya ce. “Momy ki fada mata tun yanzu Wallahi ba zan bari taje ba” Ban da Murmushi babu abunda Momy take har Ataa ta kai doyar ta aje ta fito rike da farce, da alama ta yanke ne.“Ataa babu zancen zuwa Abuja da ke in ji Dan wajen Fulani” Ataa ta bata fuska sosai tana murza yatsan. “To mi nai? Kin fasa zuwa da ni kenan?” “To sai mum gani dai yanzu” Momy ta tambaya tana kallon yadda take mursa hannun nata. Ban da kallon ta babu abunda Aliyu yake ban da kallonta ya lura da yadda take murza hannun. “Mu ga hannun” Kamar jira take yana cewa haka ta maida hannayen nata duka baya ta turo bako idonsa na cika ta kwalla ta nufi kofar fita, sai da ta lura da idon Momy basa kanta sannan ta murguda masa baki hawaye na sauko mata, a maimakon ya ji haushi sai ta yi mugun burgeshi har yayi murmushi ya maida fuskarsa gurin Momy wacce ta dauko masa wani zance. “Jiya an fada min ba dadi a gidansu Rahma, ta yi min gorin haihuwar wai baka haihuwa shiyasa kake dawainiya da Rahma, kuma wai Rahma ba zata koma ba sai nan da wani lokaci” “Miya kawo haka?” A nan Momy ta labarta masa komai car ciki har da zancen Ataa da mahaifiyar Rahma tai, sosai ran Aliyu ya bace duk wani abun da mace take masa yana shayewa ya kyale amman ban da taba masa family ko da kuwa kannensa ba sam baya daukar wannan balle kuma har ace Momy da kanta. “Kin fada musu gaskiya Momy, Wallahi ko Rahma kadai ta rage a gidan nan ba zan je bikonta ba, ganin damar ta ce tasa ta tafi ba dan an mata wani abun ba, and zan nunawa Rahma ko waye ni” “Bana son ka mata komai, bana son ka ce mata komai ko ka nuna mata damuwarka, abunda na ke so kawai ka bata mamaki, ka tabbar min da alkawarin da mai musu kuma ka cika min burina na abunda nai niyar hadawa” Kallon rashin fahimta ya yi mata. “Kamar ya?” “So na ke ka kara aure...!” Shiru yai for a while maganar Momya ta masa nauyi duk kuwa da shi kansa ya san yana bukatar auren, amman wa zai aura? Shi kwata kwata be taba kawo zancen zama da mace biyu a rayuwarsa ba, but if wannan hanyar ce zata saka Momy ta huce haushin abunda Mahaifiyar Rahma tai mata dole ya yi, ko dan ya nunawa Rahma he can live without her and to avoid zina da alfasha.“Idan karin auren ne abunda kike so consider it done, zan kara auren daman burinku kenan ke da Mama Fulani” “Na jidadin hakan, wannan kadai zaka yi ka saka Rahma ta shiga hankalinta, kai ma kuma ka samu rayuwar da kake muradi domin sai ka auri wata ne zaka gane wacece mace wacece muna mace” Murmushi yai ya mike tsaye ya nufi dinning. “Zan baka sati daya ko biyu ko sama da haka ka nemo wacce kake so, ka ga sai a hade aurenku da Muhseen ma” Momy ta fada tana binsa da kallo shi kuma ta juyo yana kallonta. “Muhseen ya fitar da mata ne?” “No ba Ataa yake so ba?” “Zan dauki lokaci kamin nai auren ne?” “Ni da na ke son ka y again and a xuiin watan nan ma” “Amman kike cewa Muhseen ya auri Ataa yanzu? Waya ba shi ita? Yarinyar da zan saka ta a makaranta ta fara karatu yanzu ita kike cewa Muhseen ya aura?” “Ai zata iya karatu a gidansa zai kula da ita” “Wallahi Momy Muhseen ba zai auri Ataa ba, indai ba son jefa rayuwar yarinyar nan kike son yi ciki matsala ba, karki aura mata Muhseen ko an yi auren nan ba karko zai yi ba” “Idan tana son sa fa?” “Bata san sa bata san wanda take so ba, ita kanta bata san waye ita ba balle kuma ta san wa take so a haka da take, kuma Muhseen ba dan Allah yake son ta ba, kyauta ne kawai yake rudarsa kuma kin sani Mama Fulani ba zata bari ya aureta ba, lalata mata rayuwa kawai zai yi” “Samun wanda zai auri Ataa a yanzu saboda Allah yana da Wahala ai, yarinyar da ba a san waye nata ba? Yar talakawa kamar yadda Rahma da iyayenta suka fada, kara ma Muhseen din dan kyauta kawai yake sonta wani ma neman fasikanci zai yi da ita ai kara a aurarda ita tun kamin wani ya lalata mata rayuwa domin ba wani wayo da ita ba” “Momy wai mahaifiyarta tace miki tana son aurarda ita? Ki bar yarinyar nan ta fahimci miye duniya tukuna, dan Allah mu bar maganar nan, kuma karki da ita Abujar nan dan girman Allah Momy” Ya karasa rai a bace gaba daya ransa ya gama baci, maganar Ataa na zuwa ganin Kamal da kuma zancen Momy ga kuma wannan maganar da wani Muhseen. Kasa cin komai ya yi a dinning din sai kallon kanensa da ke cin abincin yake domin Momy tuni ta tafi bangaren Daddy dan kai masa na shi breakfast din. Tashi yai ya fice daga falon ya dawo cikin motarsa ya zauna sannan ya kira Nasir ya labarta masa abunda ya faru. Dariya Nasir ya saka masa kamar wani mahaukaci. “To kai yanzu miye matsalar da soyayyarta ta Muhseen?” “Nasir ba san yadda na ke ji ba na, yarinyar nan bata sam ciwon kanta ba ba ta ma san waye ita ba, karatu ne abunda na ke son yarinyar ta samu a yanzu, that's why na kira ka samo wani mai koyarwa ya rika zuwa gida yana koya mata boko idan ta fara fahimtar komai yadda ya dace sai na kaita makaranta, islamiya kuma zan saka ta ta su Siyama” Har yanzu Nasir dariyar Aliyu yake, ya san son Ataa yake shiyasa yake kishinta amman jin kai da kasaita ta hana shi fahimtar hakan, wata kila kuma ya fahimta kawai dai baya son nuna ne dan kar a masa dariya, irin yadda ya tsari talaka ace ta kai har ya fara son wata yar talaka.“Za a nemo wani malamin, amman ka san shekaranjiya ma Kamal din yake tambayata ta whatsapp wai ina yarinyar abokina” “Ka rantse” “Wallahi, har yake cewa ya san abunda yai be kyauta ba, amman wai ransa ne ya bace kuma abunda Mama Fulani tai bata kyauta ba” “Sakaren banza har yana da baki yanzu stupid” Nasir yayi dariya. “Shi ma ai yana son ta ne kamar” Tsaki Aliyu ya ja ya katse kiran yana rika sitarin motar, sannan ya lalubo number wani abokinsa wanda ya san yana fannin makaranta ya kira shi ya fada masa cewar yana son a sama masa wanda zai rika koyar da wata karatu a gida, domin ganin yake Nasir be dauki abun serious ba, and idan ba karatun ya sakawa gaba ba yana ganin kamar Momy zata iya daukarta ta bawa Muhseen amman idan ta fara karatu dole zata kyaleta. ATAA POV. lokacin da na bar falon da kuka na fito zuciyarta cike da jin haushi Aliyu da nasan cewar hana tafiyar zai yi da tun farko ban fada masa ba. Gurin Nana na dawo lokacin tana balcony zaune ni kuma na wuce dakin na hau kan katifa na kwanta ina ta kukana a hankali dan bana son Nana ta ji. Ina jin lokacin da Momy da kanta ta kawo mana abun karya har ta zauna kusa da Nana tana tambayar ina na ne. “Ya sega ciki dazun ya shiga ta kwanta” “Ko ta yi fushi ne saboda na ce ba a a Abuja da ita ba?” “Abuja?” “Murna za muje yi to tace zata bi mu amman yanzu Yayansu ya zo ya ce ba za a je da ita ba, wai ba zata je ta barki haka ba” “Ataa haka yake ai wani lokacin da haurin hutsi amman nan da nan ka sauka” Ban san abunda ya bawa Momy dariya ba har sai da tai magana bayan gama dariya. “Ke har yanzu hausarki bata gama fitowa ba”Sai na ji Nana ma ta yi dariya ta ce. “Da san kai baka iya hausa ba, baka ji hausa ba sai faranse sai buzanci, kadan kadan ka fara jin hausa har ka ji ka sosei sosei” “Amman kin ga Ataa ita ta iya hausa sosai sam ba zaka ce ma tana jin buzancin ba in ba dan kammani ba.” “Ataa ya tashi cikin hausawa, tun kuna kamba kai da babanka har ka zauna argungun har ka dawo sekoto, Ataa da Lukman mai mutuws duk ka ji hausa sosei” “Ku yan wani gari ne Nana? Na ji kin ce kun zauna kamba?” “Daga Agadez ka gudu doso daga doso ka zo kamba sai ka yi argugun ka yi bodinga ka yi sokoto, kana ta yawa yawa yawa kai da mai gida na mu” Momy ta dade tana fira da Nana a nan na ji cewar a ni a kamba aka haife ni Lukman kuma a sokoto, wanda da duk ban san da hakan ba, domin ni na yi wayo ya bude ido na ganni a sokoto ne kawai kuma ban taba tambayar dalilin zuwanmu ba balle inda aka haife ni. “To amman miya kawo ku garin nan na? Miyasa kuka baro garinku Agadaz?” Daga wannan tambayar da Momy ta yi ma Nana ban sake jin Nana ta ce koma ba har na tsawon lokaci, can kuma na ji Nana ta ce. “Labarinka ba se da dadi ka ji ma kunnenka, baka son kana tuna baya ba se da dadi ka ji, amman kai babban mutum ne mai kima da gima amman yanzu ba shi da amfani, ka koma kai kadai mijinka ya tafi ya barka dan ka ya tafi ya barka yanzu ka koma kai kadan sai Ataa” “Muna tare da ke Nana, sanin wacece ke ba shi da amfani ma yanzu kuma na jidadin da aka samu Ataa ta hanyar aure, shine babban farin cikina” Shine abunda na ji Momy ta fada kamin Nana ta dora da nata tana ɗaɗa hannunta. “Ahhh Ataa yana da ubanta mai kyau kyau kyau kyau sosei, kai ne Ataa ta biyo ai, uban Ataa kana da kyau kana da fari kama da gasi kamat balaraba” “Allah sarki Allah ya jikanshi, ashe Ataa shi ta biyo domin na lura yata ta fiki kyau sosai, bari na leka bangaren Daddynsu na bar shi shi kadai” Daga haka na ji ficewar Momy faga bq din ni kuma na taso na share ragowar hawaye na fito na zauna kusa da Nana na rumgumeta, cewar Ni kadai na rage sai ita ya taba min zuciya, ban taba tambayar dalilin zuwan mu nan ba, da kuma rashin kowa a nan ba, domin ban tana kawowa rai komai ba, kuma na lura kamar Nana bata damu da hakan ba, sai yanzu ina da bukatar ji domin na lura yan'uwa suna da rana ko da kuwa talakawa ne na tabbatar da ace wani nata yana kusa da ita da bayan ni da Doc Asim be isa ya mata haka ba. Da yare buzanci ma kalleta ina murmushi na ce. “Nana idan kin kara jin sauki sosai za mu tafi gida can Agadez gurin danginki ko?” Sai ta girgiza min kai. “Aa ba zan taba zuwa ba har abada, Babana ya yi fushi da ni, na bashi kunya ba zan iya komawa garin nan ba har abada, sai dai ke kije idan na mutu” Ban sake cewa komai ba ganin hawaye a idonta, tabbas ba dadi ne ya saka ta baro garin ba, wata kila wanin abun ta aikata ko kuwa korarta yai oho.Da rana Amina ta kawo mana abincin rana jalof din taliya da kifi an saka mata koren wake da wasu abubuwan da na zan iya tantance su ba, sai kamshi take mai ya kwanta gwanin sha'awa. Bayan mun gama ci na shiga bandakin nai wanka daman Nana tun da ta gama karyawa safe tai nata, ina fitowa na dauki rigar dazun na saka n zauna kaina babu dankwali daman na fi sakewa a haka. Can da la'asar sai ga Amina ta sake dawowa, wai na fito ana kirana ban saka komai ba na fito daga ni sai doguwar rigar jikina na biyo bayanta na yi zaton Momy ce take kirana sai na ga wani mutum cikin shiga ta kamala zaune a amman wata kujera hannunsa rike da wata katuwar waya. “Zauna nan” Na zauna a empty chair da Amina ta nuna min sai ta wuce ciki, ni kuma na gaishe da mutumun ya amsa min da fuskar far'a, ya soma tambaya inda na tsaya a karatuna na boko daga nan na gane cewar malamin boko ne. “Aji hudu na tsaya a yakubu mu'azu, ban sake yi ba” “Kin iya karanta hausa?” “Eh na iya karanta hausa ko wace iri, da numbobi” “Ban iya ba” Sai ya miko min wayar hannunsa ya ce na karanta hausa. Gata ne a rubuce a take na soma karanta ta sai dai ina yi ina gargada wani gurin kuma sai ya gyara min idan na fadi wani abun ba daidai ba sai yayi ta min dariya, bayan na gama ya bani turanci ya ce na karanta sai na kafaranta da hausa ba tare da san ma'anarsa ko fassararsa ba, nan ma ya sha dariyata ni kaina na yi dariyar kaina domin duk turancin da ya nuna min da hausa na ke karanta shi. Muna cikin haka Aliyu ya fito tare da Momy ashe wai yana cikin gidan ni ban ma sani ba. Mutumen ya shiga masa bayani “Ba laifi tana da kai kuma ta yi kokari sosai, yanzu hausar ce za a dora ta akai sai kuma turancin da zamu fara daga farko domin shi tace bata iya komai a ciki ba” “To yayi kyau” Ya fada fuskarsa ba yabo ba fallasa, sannan ya saka hannunsa aljihu ya ciro kudin da ban san ko nawa ba ne ya mikawa mutumen. “Ga wannan ka hau mota za mu neme ka?” Karba yai yana godiya ya karbi wayarsa da ke hanuna yai min sallama ni da Momy fuskarsa da murmushi ya nufi gate. “Be yi ba ba ne?” Bayan ya wuce Momy ta tambaya. “No na cika sakewa bana son namiji mai sakewa da mace sosai” Ya fada yana kallona. “Ba na ce ki daina fitowa haka ba?” “To ai hijab din ya yi datti duka kayan sun yi datti” “Je ki sako Hijab dinki” “To ba ya wuce ba?” Na fada ina turo baki. Harara ta yai sai Momy ta ce. “Ataa yata idan Aliyu ya ce ki yi abu ki rika yi ki daina masa garda kin ji? Je ki saka wata kila rakiyarsa za ki yi” “Tau” Tashi nai naje na saka hijab din na dawo, ko da na dawo yana cikin mota ya bude front seat da alama ni yake jira, shiga nai na zauna da gangan na ki rufe motar sai ta ya mika hannunsa ya janyo ganbun ya rufe sannan ya soka taka motar daman tuni aka bude masa gate.Ba mu yi wata lafiya mai nisa ba, muka iso gaban wata katuwar makarantar islamiya, wani irin dadi ne ya lullube na kalleshi da sauri. “Saka ni za ka yi?” Sai yai min banza kamar be san da zama a cikin motar ba, ya bude motar ya nufi wani bangare na makarantar ya bar a ciki, be dade ba ya dawo ya bude min murmushi motar da kansa na fito na tsaya a kusa da shi ya wani hade rai irin kar na ga damarsa din nan, wani malamin ne ya zo ta takardu ya ya tambayi sunana da sunan Baba lafiya ta da sauransu sai ya rubuta a form din hannunsa dabya bukaci number waya sai Aliyu ya bada tasa. “Shikenan yanzu sai uniform za a siya mata da kuma hotonta da za a laka a jiki” “Ana siyar da uniform din a nan” “Akwai muma siyarwa dinkaken ma ne” Be tambayi nawa ba yake ba kawai ya saka hannunsa aljihu ya ciro kudin masu dan dama ya mikawa mutumen. “A bata uniform din ka rike canjin ka cire kudin form din hoto kuma za muje ayi yanzu, dan Allah ka saka ido akanta bata iya komai ba, tun daga farkon fari za a fara koya mata komai” “In-Sha-Allah ba ka da matsala, ba ri a dauko mata uniform din” Komawa yai cikin makarantar ya dauko uniform din cikin wata farar leda ya miko min na karba ina wani irin murna kamar na zuba ruwa a kasa na sha. Sannan na koma cikin motar shi ma Aliyu ya zagayo ya shigo yayi mata key. “Na gode na gode sosai Allah ya saka maka da alheri” Be amsa ni ba ko inda na ke be kalla ba, ni kuma ban damu ba farincika ya gama cika zuciyata gaba daya, daga ilslamiyar ya wuce da ni gurin daukar hoto aka dauki hotona aka ba shi, fiye da kudin hoton ya bawa mutumen, abunda na lura da shi idan zai maka alheri ko ya baka hakkinka sai ya ninka maka ko kuma ya baka abunda ya fi yawan nawa, na yi zaton daga nan gidan za mu koma sai ya nufi AGG da ni, ban taba shiga shagon ba tun da nake ganinsa sai dai kawai na bi an wuce amman har bara na yi a gurin shagon lokacin da nake tsananin bukatar kudin nan. Yana gaba ina binsa a baya sai rabon ido nake ina kallon kayan shagon ina ta kalle kalle da kansa yake zabon kayan ciki, yawanci gowns ne na abaya da riga da skirt na kanti, sai takalmi masu kyau ta ki hudu, sai da ya biya kudin sannan suka saka masa a mota muka fito muka shiga motar ya dauki hanyar wata plaza da ni, wannan karon a motar ya barni ya shiga ciki domin be bude min dan na fito kamar yadda yai min dazun ba, ni kuma na zauna a cikin motar har yayi abunda zai yi ya fito wani na riko masa manyan ledodi.A bayan mota aka saka masa musu sannan ya shigo motar yana cin wani abu mai kamar chocolate kuma ba chocolate ba, ya ci kusan rabi sannan ya miko min sauran sai na karba na saka gefen hijab dina na goge kufan bakinsa sannan na ci, ido ya saka min yana ta min kallon rainin wayo sannan ya tashi motar muka kama hanyar gida ana kiran sallah magariba. A harabar gidan ya faka motarsa ya bude boot din ni kuma na bude na fito rike da uniform dina zan tafi bq sai na ji ya ce. “Wa za ki bar wa wadannan kayan?” Dawowa nai na dauki ledodin na yi zaton cikin falonsu za a shigar masa da su sai na ji ya ce. “Leda ukun ne na ki biyu Mamanki ne” Na zaro ido ina bude baki. “Da gaske da gaske” “Da karya” Na fada ba tare da ya kalleni ba ya rufe boot din ya nufi sashen Momy, wani tsalle nai na dire rai na fes, a gaskiya yau Aliyu ya burge ni domin na kura shi ma yana da mutunci kamar Kamal sai dai Kamal ya fishi son mutane da far'a. Nana ma ta yawa sosai da ganin kayan da kuma halin Aliyu daman tun muna asibiti take ta yabonsa tana ganin kirkisa sosai, wannan karon har da cewat tana mamakin yadda hake ga hidima da ni haka. Bayan sallah isha'i Nana ta ce na je na masa godiya kuma na ce ita ma tana masa godiya. Rigar jikin na cire na saka daya daga cikin Egypt abaya da ya siya min na saka na yafa mayafinta sannan na nufi part din rigar sai kyalkyali take ko'ina na jikinta. Da sallam na tura kofar falon na shiga, sai Momy ta amsa min da far'arta Aliyu yana zaune saman cushion ya hade rai sosai kamar an masa wani abu, ina juyowa sai na Muhseen tsaye yana sakar min murmushi. “Laaa Ya Muhseen” “Pretty na” Ya fada yana kallon yadda rigar ta karbe abun ka da farin mutum ya saka babaken kaya.“Yaushe ka zo?” “Yanzu nan, jiya na ban ji a waya ba kuma ina da bukatar ganinki shiyasa na zo, ya kike?” “Lafiya kalau” Na amsa ina dariya kamar an min wani abu, ni dai har ga Allah ina son mutum mai far'a da dariya kamar Kamal da Muhseen, sai dai Kamal ya fi kwanta min sama da Muhseen din kuwa da kasancewar shi ma yana min far'a sosai, kusan sai na ce duka suna burgeni kuma ina son su. “Kin yi kyau pretty na rigar ya karbd ki” Ya fada yana rika rigar nawa ya buda ta tai fadi. “Eh dazun Aliyu ya siya min ita Nana tace na zo na masa godiya” Yanayin fuskar Muhseen na ga ta canja sai ya dan wara ido yana zolayata. “Hop kin daina sake jikinki dai domin na lura ana sake miki da yawa” “Sake jiki kuma?” Momy ta tambaya sai ya kalleta “Yes, lokacin da take Abuja a garden take wanka, a gareji take canja tufafi sai da na mata magana” Juyowa Aliyu yai ya kalli Muhseen yana lilo da kafarsa wacce dayar ki saman daya. “Ka ganta kenan? Shiyasa ka ce kana son ta?” “Idan ma haka din ne ai ban yi illa ba” Tasowa Aliyu yai daga saman kujerar da yake zaune yana fadin. “Ataa ba ki da hankali kuma kurciya na damunki, Momy kina ganin abunda na ke fada miki ko? Ya ganta tana wanka ta na canja tufafi kuma shi ne yanzu a tsaye a gabanki har kina amsa dariya? Wallahi baki san ciwon kanki sam” Muhseen yayi murmushi har zai yi magana sai muka hi Aliyu ya kyalkyale da dariya mai karfi wacce ban taba zaton bakinsa na iya irin wannan dariyar ba. “Magana ta fito Muhseen kana son Ataa saboda ka ganta a sirara, Wallahi wannan nuna mata rashin daraja ne da raina mata hankali, what a shame lallai kai yaro ne kuma wawan duniya tun da har tsiraicin yake maka sha'awar kallo what a sad” Yana fadar hakan ya fice yana dariya dariya irin sosai din nan kamar ba ta hankali ba.ALIYU POV. Duk wata dariya da yake na fuska ne kawai amman ransa cike ya ke da bacin rai da bakin cikin jin cewar Muhseen ya taba ganin Ataa tsirara wani abun yaji marar misaltuwa har yana jin kamar kirjinsa zai rabe biyu, sai kuma ya ji kamar ya danne Muhseen ya cire masa idanuwa. Be san abunda ya kawo shi yau ba ma, gashi yana cewa ba za a tafi da Ataa abuja ba saboda shi da Kamal shi kuma yazo yanzu. Yana faka motarsa harabar gidan sako na shigowa wayarsa, ganin sunan Rahma yasa shi budewa domin baya cikin mood din saurare kowa a yanzu. _I'm sorry akan abunda ya faru, Mommy ta yi fushi ne sosai shiyasa amman dan Allah ka yi hakuri, kuma ina neman izininka zan tafi Dubai jibi_ “Really?” Ya furta bayan ya gama karanta sakon. “You will regret this Rahma ke da iyayenki” Ya fada sannan ya bude motar ya fita zuwa cikin gidansa, haka ya kwana a gidan cikin wani irin yanayi na bacin rai tsakanin wanda Rahma tai masa da abunda Muhseen ya fada sai ya rasa wanne ya fi masa zafi. Ko da ya tashi da safe kansa kamar zai tsage sabar bacin ran daya kwana da shi jiya, he feel unsafe sai da yai wanka ya shirya cikin wasu tufafin ya dauki hanyar arkilla tun da farar safiya haske ma be gama bayyana ba. Ko da ya shiga falon babu kowa sai ac da wutar da aka kunna, but he got lucky yau Momy a part din ta tai sallah asuba after Daddy ya tafi masallaci ita kuma ta dawo part dinta tai sallah, daman ta kan yi haka wani lokaci wani lokacin kuma acan take yin sallah ta. Tura kofar dakinta yai ya shiga ba dan ya tabbatar tana ciki ba, idan ma bata ciki shi zai kwanta a nan ne for a while hankali zai fi kwanciya ace yana gidan fiye da yana can dabam. Zaune ya same ta saman carpet karbin a hannunta tana ja. Ita kanta ta yi mamakin ganinsa da safen nan. “Lafiya dai?” “Lafiya kalau Momy ina kwana” “Lafiya Kalau, amman ba lafiya na ka zo da safen nan” Ya yi shiru na wani lokaci sannan ya ce. “Momy wai Rahma ta turo min sako zata je Dubai” Da mugun mamaki Momy ta kalleshi. “Dubai? Da izinin wa?” “Wai izini take nema” “Uhmm Wallahi Rahma nan ta maida wani sholobiyo, daman tun farko kai ka nuna mata fita ba da zininka ba ai, yanzu kuma ganshi ba nan, maganinta kamin ta dawo ka auri wata Wallahi” “Yes nima abunda na kwana da shi a raina kenan” “Haka ma za a mata, kuma idan zaka bi nawa Ataa na ke son ka aura wacce ta raina take ganin ba komai ba ce” Kamar saukar Aradu haka Aliyu ya ji maganar Momy, Ataaa Ataaa Ataaa Ataaa sunanta na ta maimaita kansa a kunnensa, da sauri ya kalli Momy. “Momy Ataa?” “Yes” “Amman..... ” Sai kuma ya mike tsaye ya saka hannayensa aljihu ya daga kansa sama yana shakar iska kamin ya sauke ya juyo ya kalli Momy. “Momy seriously?” “Yes don't you like her?” “I do, but.....” Sai murmushi ya subuce masa ya shafa kansa. “Momy ke kike fada min wannan da kanki? I can't believe this” Murmushi Momy ta yi. “Do you love her?” Shiru yai na wani lokaci yana sauraren yadda zuciyarsa ke mugun bugawa with full farincikin da be daga ina yake sauko masa ba. “Momy wasa dai kike min?” “Indai tana son ka da gaske na ke yi” “Zata so ni mana Momy ai ita bata san so ba, zan koya mata komai Momy trust me” Ya fada yana dukawa ya kama hannayenta duka biyu ya rike, shi kanshi sai yanzu yake jin cewar son Ataa yake yi, duk wani abun da ya dade yana jinsa akanta sai yanzu kullin ya watse a jikinsa da zuciyarsa, domin tun da ta zo duniyarsa sai yake jin kullum kamar a takure yake. ZAKI By Khadeeja Candy 39... Kamar an diga man kuli a cikin ruwa mai mugun sanyi haka Aliyu yaji jinin zuciyarsa ya taso yayi tsama saboda kalaman Muhseen. “Kai Pretty wai kin duba madubi yau ko? Gaskiya Allah ya iya hallita” Cewar Muhseen yana kara kallon yadda uniform din yai mata mugun kyau kasancewarsa Maroon color, ga gashin kanta data sakawa ribbon ya sauko har bayanta gwanin sha'awa. Ko wace kalma ta Muhseen Aliyu hade ta yake da yawun bakinsa, ba kuma iya yawun ne kawai yake hadewa ba har da abunda yake ji yana taso masa yake dannewa, shi kanshi ya san yayi abunda ba zai iya ba, yana tsaye wani na yaba kyau matarsa. “A a ba mu da madubi ai” Ataa ta fada tana murmushi. “Zo na nuna miki kanki a wayana” Ya zauna a kujerar da ke kusa da shi yana ciro wayar daga aljihunsa na gaba, bata zauna din ba ta juyo ta kalli Aliyu wanda idonsa ke kan wayarsa tunawa da yace ta daina sakewa Muhseen. “a a bari na je na duba a Mota” Ya fada sannan ta fara takawa zata wuce Muhseen ya bi bayanta da kallo komai na jikinta motsi yake a cikin uniform din kasancewarta mai tubultubul kuma uniform din ya dan kama jikinta din jiki ga shi bata da komai a ciki, da gangan yai hanzarin kai hannunsa ya kama gashin kanta ya juyo da ita ta rika yatsun hannunta. “Pretty ina zoben da na baki...?” Bata amsa shi ba tai saurin fisge hannunta tana kallon Aliyu hankalinta a tashe kamar wacce za ayi ma wani abu. “Muhseen....!” Aliyu ya daka masa tsawa a cikin muryar da shi kan shi be san da zamanta ba. “Karka sake kuskuren yabon kyau Ataa balle ka ce zaka kai dan iskan hannunta ka taba ta, wannan ya zama na karshe ina nufi na karshe....” Magana Aliyu yake ma Muhseen cikin tsawa yana nuna Muhseen da yatsansa kwayar idonsa gaba daya ta canja ta rine kamar ba shi ne da farin ido ba, shi kan shi Muhseen sai da gabashi ya fadi domin ya razana sosai da yanayin da ya ga Aliyu. Kamar kyalftawar walkiya haka Ataa ta bace bat a cikin falon kamin ta isa Bq har da gudunta, ganin irin tsawar da yai ma Muhseen da yake kanensa kuma dan'uwansa to ita kan ta san nata dukanta zai yi. Da sauri Momy ta fito daga kitchen tana kallonsu, kannensa ma Amina, Siyama da Husna duk sai da suka fito daga dakunansu jin yadda falon gaba daya yake amsa muryar Aliyu. har be janye yatsansa daga nuna Muhseen da yake ba sai rawa yatsan yake kamar zai da ki Muhseen da hannunsa.Wani irin abu yake ji yana masa yawo cikin jini wanda be taba jin irinsa ba, duk wani kishin Ataa da yake a can baya na yanzu ya ninka shi ninkin ba ninkin, ya yaba kyauta ya janyo gashinta kanta ya rika yatsanta, tunawa da irin kallon da yai mata da kalamansa na jiya sai ya ji kamar an yanga tsagen jikinsa an zubar a kasa, har lokacin Muhseen be iya cewa komai ba banda kallon kallon da suke da juna shi da Aliyu. “Wai miye haka ne? Shikenan idan kuma abuja hankalin Fulani ya tashi idan kuma kuna nan nawa ya tashi? Wannan wace irin rayuwarce?” Aliyu ya juyo ya kalli Momy. “Ki fada masa ya daina shiga gonata” “In daina shiga gonarka ko ka daina shiga gonata? What kind of nonsense is this, idan ina yaba kyau Ataa ko magana da ita ko taba ta miye matsalar ka da wannan?” “Babu har sai ka sake” Aliyu ya fada yana daga masa gira sannan ya fice daga falon zuwa bq. “It's because tana gidanku?” Muhseen ya fada a fusace yana bin Aliyu da kallon haushi. “Muhseen nan mu ba gidansu ba ne, gidanku ne” “To idan ba shi ba Momy miye ruwansa da ni? Naga dai ba shi da alaka da ita kamar yadda ni ma ba ni da, kuma son Ataa na ke son ta na ke be isa ya hana hakan ba... ” Amina ta kalli Momy Momy ma ta kalli Amina kamin ita Aminar ta juya ta koma cikin dakinta. “Na rasa gane kan Aliyu” Muhseen ya sake fada. “Ka yi hakuri Muhseen zan masa magana, ka yi hakuri dan Allah” Maganar da Momy ta masa ce ta saka ya zauna saman kujera yana ta huci da mamakin yadda Aliyu yake son masa fin karfi. ALIYU POV. Tafiya yake yana kamar ba kasa yake takawa ba shi kan shi be taba jin kanshi a cikin irim wannan yanayin ba kamar yau. Ji yake kamar ba zai jure wani ya kara yabon kyau Ataa ba, ko da mace ce balle namiji. Yana shiga bq din Ataa ta daka tsalle tana ihu ta yi bayan Nana da ke zaune ta boye gabanta sai faduwa yake ta yi zaton ko dukanta Aliyu ya zo ya yi, duk da bata tsoronsa a yanzu amman tana tsoron yanayin da ta ganshi a yanzu. Yayi kokarin sauke fushinsa ya dan saki fuska sannan ya taka balcony din yana isa bakin kofar dakin da Nana take ciki ya tsaya ya cire takalminsa sannan ya shiga, risinawa yai har kasa kamar jiya ya gaishe ta ya mata ya jiki ta amsa masa fuska a sake Ataa na bayan Nana zaune tana dan lekoshi ta kawar da kai. “Dan Allah Mama kar a sake bari Ataa ta fita tsakar gidan nan babu mayafi a jikin, kin ga akwai aljannu masu shiga jikin mutum gidan be rufe jiki ba, ko ka rufe ma ya aka kwashe balle kuma ba a rufe din ba? Yana da ta rika rufe jikinta da gashin kanta” “In-Sha-Allah zai rega sakawa, muna goziya jiya kaya sun zo masu kyau Allah ya biya” “Amin” Yana amsawa da amin ya mike tsaye yana watsawa Ataa wata uwar harara domin mugun haushinta yake ji kamar ita tace Muhseen din ya kama hannunta ya rike, ita kuma ta murguda masa baki ta buya bayan Nana.ATAA POV. Yana fita na fito daga bayan Nana na zauna daidai ina turo karamin bakina. “Wai shi baya son ya ga wani na min far'ah ko muna wasa ko magana, ya fi son ya gan ni cikin bacin rai, idan yaga wani ya sakar min fuska ji yake kamar an masa ruwan mutuwa a zuciya” Da yaren buzanci na fada cikin mugun jin haushinsa. Dariya Nana ta yi tana kallona ta ce. “Tunda ba ya so ai sai ki daina, namiji baya jindadi idan yana ra'ayin mace yaga wani namijin na kula ta” “Wacan zai ra'ayina? Wallahi duk ya bi ya tsane ni ban san abu da nai masa ba, bayan ma ni na fi dacewa na natseshi” “Ki tsane shi aka ce mi? Ai baki da wata hujja ta tsanarsa, domin ya gama mana komai a duniyar nan” “Haushi na yake ji kila ma dan yaga na fi shi kyau ne, sai wani ji da kan banza, kuma sai na kula Muhseen din haka kawai sai na yi ta shiga kunci ina bakin rai kamar shi, haka jiya ya kori mai koya min karatun nan da ya zo, wai ya cika far'a ya fi son ya ga ina ta bakinciki, shi fa dariya ta bakinciki take saka shi mtchhhhhhh” Na karasa ina jan tsake har ga Allah yau kan Aliyu ya ba ni haushi, ban san abunda na tsare masa ba yake bakincikin ganin dariyata, wani lokacin ma sai yai ta abu kamar ba shi ba, dazun da naje tambayarsa ai dariya yai min, jiya yai min siyayya har ina jindadi amman yau ya canja kamar ba shi ba. Murmushi kawai Nana take tana kallona kamin ta koma murza yatsun hannunta. “Yanayin yaron nan yana tuna min da mahaifinki, haka yake kishi a lokacin da yake so na, ni kuma ina kishinsa saboda kyausa, idan yayan manyan sarakai suka zo nema na ranar ba zai yi bachi ba, saboda yana jin kamar zai rasa ni” Ta fada da yaren buzanci hawaye na sauko mata, sai na kara matsawa kusa da ita na kwantar da kaina jikinta, sai ta shafa kan nawa hawayenta na sauka a kumatuna. “Mutuwa ba tai kyau ba” Ta fada da hausa tana son fashewa da kuka. Nima hawayen na soma yi tunawa da Baba na na san da yana raye duk wannan rayuwar ba mu shige ta ba, balle har Aliyu ya nemi takura domin Babana yana so na sosai. Ganin ina hawaye yasa tai saurin share nata kukan tana dariya kamar ba ita ba. “Yana can cikin rahamar Allah In-Sha-Allah” “Eh Nana yana cikin Rahama Allah ya jikanshi” “Amin”Sanye da uniform Siyama ta kawo mana abun karyawar mu bayan ta gaisa da Nana ta fito daga bangaren mu ni kuma na biyota ina tambayarta ko nima zan iya zuwa makarantar. “A a yau ba a zuwa sai da yamma, ai ita Islamiya sai assabar da lahadi kawai ake zuwa da safe” “Na sani, amman na ga wata islamiyar idan mutum baya zuwa makarantar boko sai ya tafi islamiyar safe” “Wannan ba a zuwa” “Sai kin dawo Allah ya tsare” Na fada ina kallonta gwanin sha'awa, sannan na juyo na dawo bq din na soma cire uniform din ina tunanin maganar Nana ta dazun wai idan yayan manyan sarakuna suka zo sai yai ta kishi, lallai Nana ta yi farin jini tunda har da yayan sarakuna sukai nemanta. MUHSEEN POV. Yana zaune a falon har Aliyu ya fito daga bq ya shiga motarsa ya dauki hanyar gida. Tunani yake ta yi yadda Aliyu ya zo rana tsaka yake son hana shi kula Ataa, idan ma wai wani sonta yake to shi mai gaba daya zai yi idan take takensa kenan shi zai fito kai tsaye ya aureta ya ga yadda zai yi. Har Momy ta gama hada breakfast din ta zubawa Siyama ta kuma zuba na su Nana ta bawa Siyama ta kai musu Muhseen na zaune a gurin be huce ba, a dinning ta jera sauran ta fada masa ya tashi ya karya sannan ta wuce bangare Daddy dan kai masa na shi su karya tare. Bayan ta gama da Daddy ta sallame shi ya wuce gurin aikinsa ta dawo part dinta sai ta samu Muhseen zaune a dinning shi kai yana cin plantain a hankali kana ganinsa kasan hankalinsa baya jikinsa, shi kai ne a dinning din hakan na nufi Amina da Husna sun gama karya sun tafi shi kuma ko rabi be yi ba. Sai da Momy ta kai kulolin data dauko part din Daddy kitchen sannan ta dawo dinning din ta ja kujerar da ke fuskantar ta Muhseen ta zauna. “Ba ka ci abincin ba?” “Momy ina tunanin ya kamata na fadawa Abbah da Daddy zancen Ataa kara su san da maganar, idan ma karatun za tai ko wani abu sai tai a gidana, ko waje ta kama sai a fitar da ita ai” Momy ta dan yi shiru na waji lokaci tana sauke ajiyar zuciya. Kamin ta kalli Muhseen a natse ta fara magana. “Shekaranjiya na tafi gidansu Rahma gurin bikonta, wai ta yi yaji ta tafi gida saboda mijinta na kula Ataa, nemawa mahaifiyarta magani da zuwa dubata da yake sai Rahma ta dauka son ta yake, shi ne tai fushi ranar da na je bikonta ni da kawata babu kalar maganar da mahaifiyarta bata fada min ba saboda Ataa, tana kiranta da yar talakawa yar bara a titi wai yar su ba za ta yi kishi da Ataa ba” Tun da Momy ta soma maganar Muhseen yake kallonta dan shi be ga ta inda wannan abun ya shafe shi ba, domin ba matsalar wani ce yanzu a gabansa sai ta shi.“Gaskiya Rahma bata kyauta ba, kuma be dace tai haka ba, cewa akai Aliyun son ta yake ne?” “Ni kaina ban jidadin abunda mahaifiyarta da ita Rahma kanta su kai na tun farko, kuma ina tunanin tana wannan abun ne saboda tana ganin it kadai ce a gurin mijinta, shiyasa na yanke shawarar...” Sai ta kasa karasawa kamar mai jin nauyi. Muhseen ya kashe kunne sosai ya maida hankali yana saurarensa, main reason din yake son ya ji domin ya fara fahimtar inda zancen Momy na dosa. “Shawarar me?” “Wata kila Fulani ba zata bari ka auri Ataa ba, ko kuma idan ka aureta ta gallaza mata, ko wani abun ya samu kyauta wanda zai iya sakawa wata rana ka sabu da ita ko musguna mata, amman ina da tabbacin Aliyu ba zai iya juya mata baya ba ko da baya sonta saboda ya san hakkin aure, kuma mutumen da ya zauna da Rahma zai iya zama da ko wace irin mace a duniyar nan, duk wani guri da fada na Rahma da mahaifiyarta akan Ataa ne shiyasa na yanke shawarar Aliyu ya aureta ko dan gorin da suke mata na kuma nuna musu na isa da shi...!” Wani irin abu ya ji ya daki kirjinsa sai yai murmushi yaja numfashi ya sauke. “Ya fada miki cewar son iskanci nake wa Ataa ke nan? Kuma kin yarda duk da kin san ni bana neman matan banza, dan na ce ina son Ataa saboda tana da kyau ai ban yi laifi ba, kina tabbaci idan bata da kyau Aliyu ma zai so ta? Kina da tabbacin shi din Mama Fulani zata bar shi ya aureta? Kawai dai kin nuna ke kika haifi Aliyu da kanki kuma kin nuna masa son kai, kuma Ina masa farincikin samun uwa kamar ki wacce zata so abunda danta yake so har ta fishi son abun” Yana fadar hakan yaja kujerarsa baya ya mike tsaye. Tuni idon Momy ya cika da kwalla zuciyarta kuma tana mata babu dadi. “Allah shine shaidata, ban aikata hakan dan nuna son kai ba, sai dan ganin kamar Ataa zata fi samun kwanciyar hankali idan ta aureshi, kuma Rahma ta raina kanta gudun yar talaka sai ta ga ta aure mata miji ma gaba daya, idan har bana son ka ba zance Amina ta aureka ba, ba zan baka yar cikina ba Wallahi ban rike wani dabam ba, kai da Aliyu duka daya ne a gurina, na dauke dana wanda zan iya sakawa na hana, na zaba masa ko na canja masa zabi” Juyowa Muhseen yai ya kalleta. “Ashe kin dade da yanke hukunci kika barni ina da lalabe cikin duhu, ni da Aliyu ba daya ba ne a gurinki da ni ma kin dauke ni da da kin hana Aliyu son Ataa ko da zai mutu kin ba ni, domin na fishi sonta kuma na fi cancanta na aureta fiye da shi ita kanta idan kika tambaye ta zata fada miki ni take so, kin sani Momy na tun yau ba ina son Ataa amman yau ni za ki zauna a gabana ki fada min gaskiya cewar kin ba danki ita, good luck wish you all the best” Yana fadar hakan ya fice daga falon a fusace, ya bar Momy tana aikin hawaye.Sai a yanzu take jin cewar bata kyauta, sai a yanzu take jin girman kuskuren da ta aikata, da tasan cewar Muhseen ba zai fahimce kamar haka ba da bata aikata ba tun farko. Fashewa tai da kuka a gurin ta tashi da sauri ta shige dakinta, Husna da Amina suka fito suka bi bayanta jin kukanta hankalinsu tashe. “Momy lafiya?” Husna ta tambaya tana zama kusa da ita. “Sam be dace nai haka ba, yayan fulani ba su cancanci komai a gurina ba sai farinciki da goyon baya, ban za ci cewar Muhseen zai min fahimta baibaiye ba ban tsammaci zai dauki haka ba, Wallahi ban yi wannan abun dan son kai ba sai dan dukansu su samu farincikin” “Kema kin sani Momy ba zai taba fahimta ba, tsakani da Allah fa ya riga Ya Aliyu sonta, kuma shi Ya Aliyu ba ma cewa yai yana son ta ba kawai dai kina son yin hakan ne saboda Rahma, kuma ya dace ki yi hakan amman za ki iya yi da wata dabam ba dole sai Ataa ba” Momy ta dauke kanta daga barin kallon Husna wacce take maganar ta dafe kanta tana hawaye. ATAA POV. bayan mun gama karyawa, Nana ta ce na je na taya Momy aiki domin yau ko yar sharar da na ke ban mata ba, ni kuma na ki zuwa domin a tunani Aliyu yana nan kuma idan har na je sai Muhseen ya kula idan kuma ya kula ni Aliyun zai iya cewa zai min fada ko ya dake ni ma wata kila. “Zan je Nana amman sai Aliyu ya fita” “Tau idan dai za ki tafi sai ki saka mayafi” Na dan turo baki domin ni dai a cikin gida a ce ka saka mayafi yana takura min sosai. Muna haka ni da Nana na hango Muhseen tsaye a balcony yana kallon kofar dakin mu.Da sauri na tashi tsaye na fito daga dakin domin yanayin fuskarta ya nuna akwai damuwa sosai a tattare da shi. “Ya Muhseen lafiya?” “Mamaki kike ba ni yadda kika yarda ki auri Aliyu” Ba zan iya cewa wani mai maganar ba Muhseen ba, domin sautin muryarsa ne bakinsa ne yake motsu kuma shine tsaye a balcony din dakinmu, amman ta ina wannan maganar ta fito mai kamada almara, dan lekawa nai ina kallon fuskarsa to ko wani abun ya sha ko kuma bachi yai ya tashi yana mafarki? Idan ba haka taya zai furta irin wannan maganar da hankali ba zai dauka ba balle har ta zauna a kwakwalwa. “Wane irin aure kuma? Wane Aliyu?” “Kin fi kowa sanin abunda na ke nufi, amman tabbas Ataa kin ba ni mamaki ashe ba ki da tunani ba ki da zuciya kuma ba ki kishin mahaifiyarki da har za ki yarda ki auri mutumen da aka hada ba ki da shi aka cire mata koda ya dasawa matarsa? Mutumen da ya wulakantaki irin wannan mutumen za ki aura?” Mutuwar tsaye nai wacce ta fi ta kwance hadari da rikitarwa. Sam ban gane inda ya soba ba amman na gane abunda yake kokarin furtawa. “Ba ka san abunda kake fada ba Muhseen, ni Aliyu be taba nuna min so ba balle har ya furta min, kuma ba zai taba so na ba har abada saboda ya tsani talaka, ni ma kuma ba zan taba son sa ba saboda na sani dan masu arziki, babu wannan a tsakanin mu idan ma wani yai maka karya to karya ce kawai ba gaske ba” Na fada ina girgiza masa kai, tuni Nana ta taso ta fito daga dakin ta kawo bakin kofa tana kallon Muhseen. A tsawa ce ya ce “Gaskiya ne Ataa Momy ta fada min Aliyu za ki aura, mutumen da ya cirewa mahaifiyarki koda ta yi wata da watanni tana jinya, saboda kawai ya dauke ta ya kaita asibiti ya kawo ta nan be isa ya goge tabon abunda yai mata ba, domin har abada kodarta ba zata taba dawowa ba, ta koma rabin mutum ba cikakkiyar mutum ba” “Ni Ataa ni a aka cirewa koda? Ni?” Nana ta tambaya cikin yaren buzanci tana juyowa da ni dan na fuskance ta, tuni hawaye suka gama wanke min fuska a yau Muhseen ya tona abunda Nana bata san da shi ba, a yau Muhseen zai saka Nana cikin wani halin na damuwa da tunani da zullumin mutuwa a kullum.“Na tsane ka Muhseen na tsane ka, bana kaunar ka, idan ma ka burge ni kai to baka burge ni ba, kai da Aliyu duka na tsane ku, bana son ka bana son sake ganin fuskarka karka sake shiga rayuwa ta” Na fada da iya karfin muryarta ina hawaye, matsowa yai kusa da ni yana girgiza min kai sai na kada masa tsawa. “Dukan ku kuna juya rayuwata yadda kuke so saboda ina talaka, Nana bata taba sanin wannan maganar ba ayau ka tona ta ka bude komai, na tsane ka Muhseen na tsane ka” Ihun muryata ne ya fito da Momy da Husna da Amina suka shigo bq din hankali a tashe. Nana kuka take tana dafe da cikinta ni ma kukan na ke ina rike da dayan hannunta, idan ma zan mata bayani ta ina zan fara? Ya za ayi tai fahimta? Har ta kwamtar da hankalinta. “Ataa....” Muhseen na kiran sunana na daka matsa tsawa ina nuna shi da yatsa. “Karka ce min komai, ka riga ka gama fada mata cewar an cire mata koda sai me kuma? Ka riga ka fada mata abunda bata sani ba, bana son ganin fuskarka na tsaneka na ce na tsane ka” Kallonsa Momy tai ta kalleni sai kuma ta sake kallonsa. “Me ka ce mata?” “Ai ke kika bata komai Momy ke kika ja koma... ” Be kai Ayaba Momy ta tsinka masa mari, har sai da Husna tai saurin zuwa ta rike mata hannu. “Muhseen kai ba mutum ba ne, ba ka da tunani irin na mutane, kai sakare ne sha sha sha” Tana fadar hakan ta juya ta fice daga bq din a fusace ta bar Muhseen tsaye dafe da kuncin idonaa sun kade sun yo ja sosai. Sai da ya kalleni sannan ya kada kai ya fice aka bar ni daga ni sai Nana muna ta kuka babu mai rarashin wani. ZAKI By Khadeeja Candy 40.... Kuka Nana tai sosai har sai da na soma jin tsoro domin tsarkewa tana tari har na tsoron kar ta janyowa kanta wani ciwon, a take na yanke kukana na share hawayena na rumgumeta ina bata hakuri, daker na rikata na muka koma daki ta kwanta saman katifa na lulluba mata zane na fito na baro mata dakin, a harabar gidan na fito na nufi gurin da ake ajeye moto na zauna a wani gurin da wani be zai iya ganina ba. Abunda Muhseen yai min ya fi abunda Aliyu ya aikata yi min zafi a yanzu, domin Aliyu akan rashin sani ya aikata kuma ya ba ni kulawar da ta dace ciki har da taimaka min na samu ilmi, na san yanayin duka wannan ne saboda ya goge laifinsa a gurina da gurin Nana, sai dai duk da hakan hakam na fi jin sakewa da shakuwa da Muhseen saboda shi be aikata min komai ba, be kuma taba musguna min ba, sai dai Abunda yai min a yau yasa na ji na fi tsanarsa fiye da Aliyun ma. Ban san wani plan na Momy ba, wata kila ta shirya Aliyu ya aure ni ko da baya sonta saboda ya kara goge laifinsa ko kuma saboda tana so a matsayin surukarta, amman be dace ta yanke wannan hukunci ba tare da jin ra'ayina ba, wata kila tana son ta mana milkin masallaka ne saboda muna gidanta, ko kuma saboda wani dalili na ta na dabam domin na tabbatar ba ni da kima da darajar da Aliyu da kansa zai bukaci aurena ko ya furta cewar yana so na, wata kila tana son ta aura masa ni ne saboda ya rage kyamar talaka domin na lura halinta da na shi ba daya ba, idan ma har da gaske ne abunda Muhseen ya fada wata kila kuma wata ake nufi ba ni ba, a a ba ma ni ba ce sam ba zai ce ni ko da ma cilasta a kai na san ba zai amince ba. Haka nai ta sake sake na na na kulla wannan na kwance wacan har aka kira azahar, ni dai sai na ji gaba daya gidan ya fice min rai, domin zama a ciki ne ya kawo yau har Nana ta ji wannan maganar mai daga hankali na tabbatar da ace bama cikin gidan ko da Muhseen zai zo yayi maganar sai dai ya saka a masa sallama da ni idan na fito ya fada min son ransa amman ba a gaban Nana ba.Ko da na koma dakin na samu ta yi alwala tana kokari saka hijabinta tai sallah, bandakin na nufa na shiga na yi alwala na fito na shimfida dankwalina na soma gabatar da tawa sallah, bayan ta sallame ni ma na sallame sai ga Amina ta shigo da sallama dauke da kular abinci da plates da Siyama na bayanta tana sanye da uniform kamar dazun da alama bata dade da dawowa daga makaranta ba, fuskar Nana kawai take kallon wacce ta kumbura sosai. “Sannu Nana” Cewar Amina wani abun mamaki da Nana ta dago ta kalleta sai tai mata murmushi ta kada mata kai, Siyama ma ta mata sannu sannan suka fice. Matsawa nai kusa da ita na soma mata magana a hankali. “Na boye miki ne saboda kar hankalinki ya tashi ki saka kanki a damuwa, ba da sanin Aliyu akai wannan abun ba, likitan da naje neman taimako a gurinsa doc Asim shine yai wannan aikin ba da sani Aliyu ba.....” A natse na zayyana mata komai tun daga kan asibitin da kullen ni da Doc Asim ya saka aka yi da kuma neman mu da Aliyu yai ta yi har ma da konewar da kodarta tai da kuma irin kalubalen da na fuskanta a zamana Abuja. Hawaye shar a fuskar Nana tana kallona da murmushi a fuskarta. “Ba kowa ce uwa Allah ya ke azurtawa da ya kamar ki mai damuwa da matsalar uwarta da nema mata mafita ba, kin jefa kanki cikin matsala saboda ni, kina bukatar abubuwa da yawa amman kika watsar da su kika maida hankalinki a gurina, ban yi zaton samun ya mace wacce zata kula ni kamar haka ba” Ta fada tana kallona, wani dadi da farinciki na ji ya lullube ni ashe haka ko wane da na kwarai yake ji idan mahaifiyarsa ta yabe shi. Sai na kwantar da kaina jikinta ina jin wani irin shauki da rahama na uwa yana ratsani.Hannunta ta dora saman kaina tana shafani. Har na bude ba ki na yi magana sai ga Momy ta shigo cike da tsoro a fuskarka muryarta har gargada take a lokacin da take mana sallama. Ni ma amsa yayinda Nana kuma na kasa daga kai ta kalli Momy, a gaban Nana Momy ta zauna kamin ta fara cewa komai hawaye sukai mata sallama. “Ban san yadda za ki dauki abun ba, ban san da wace fuska zaki kalli abun ba, ba dan ni na haifi Aliyu ba, wallahi idan za ki tambayi kowa a garin nan wanda ya san halin Aliyu ya san rayuwarsa, zai fada miki cewar Aliyu ba zai aikata hakan ba, yes na sani Aliyu yana da wulakanci amman Wallahi ba zai taba yarda ya zalince ka ba, ba da saninsa a kai komai ba.....” Daki daki Momy ta jerawa Nana komai ciki har da dalilin hana Muhseen aurena da tai wanda shine dalilin janyo duk abunda yake faruwa yanzu da kuma dalilin aurena da take son ya yi , ashe wai gori Rahma tai mata kuma ta kirani da talaka ta ce ba za a hada ta kishi da yar talakawa ba, a zatonta Aliyu so na yake, a take na ji Momy ta kara burgeni, domin a yadda suke da kudi da arziki da suna a garin sokoto, ba ko. Wace uwa ce zata yarda danta ya aureni ba yar bara a titi wacce ba a san kowa na ta ba, na sani ta cilasta Aliyu yin hakan ne saboda kawai karancinta, tausayinta na cika min zuciya wanda na ke zaton shi ne a zuciyar Nana har ta daga kai ta kalli Momy tana hawaye kamar yadda Momy ma take nata hawayen. “Kina da damar yanke ko wane irin hukunci, ciki har da maka Aliyu kotu idan har zuciyarki ta natsu da cewar shi ne ya aikata miki komai, kuma na miki alkawari nai ko alfarmar kowa ba za mu nema ba dan a bamu gaskiya a baki rashinta, kina da damar hana Ataa auren Aliyu ki aura mata Muhseen ko wani dabam wanda zuciyarta ta natsu da shi, amman ina rokinki dan girman Allah kar ki ce za ki bar garin nan zuwa wani gari ko wani gidan dabam, ki zauna da mu dan girman Allah” Momy ta fada tana hade hannayenta guri daya tana rokon Nana.Shiru da Nana tai ne yasa Momy ta juyo gurina tana kallona. “Ban yi niyar aikata komai a gurinki ba sai alheri, dukan kudirina na kiji dadin rayuwar ki a gaba ne, ina da yakinin Aliyu zai rike ki amana, kuma zai zauna da ke ya rike ki da kima saboda yana son ki, kuma ke din kamar kyauta ce daga gurina, Allah shine shaidata” “Momy kin rike ne kamar yar da kika haifa ko da rana daya ba ki taba nuna min kyama ko banbanci da yayanki ba, lokacin da kanwar Rahma ta dake ni ki yinta ma Aliyu fada kamar ki dake shi kina fadin ba zaki dauka ba, duka wannan abun da kika min kina kara amsa sunanki an uwa ne a gurina, Wallahi na yarda da ke Momy na rike uwa ta gari.... ” Murmushi na gani a fuskarta sai ta kai hannunta ta dafa ni. “Na gode da kika fahimta Allah ya miki albarka” Tana fadar hakan ta tashi ta fice daga dakin. Nana ta bi Momy da kallo tana min magana cikin yaren buzanci. “Aliyu ya aikata kwatankwacin abunda na aikata kuma nake ganin kamar ban yi aikata laifi ba, sai ga shi alhaki yana ta bibiyana na bijerawa iyeye, cikin har da samun rayuwara a bara, da rasa kudin magani, babban a ciki shine na cire min koda ba tare da sani na ba, ko wane shafi na rayuwa darasi ne, ko wani littafin kaddara ilmi ne, da ban gudu na bar gatana ba, na bijerawa iyayena ba, da wani be isa ya nuna min yatsa ba, balle har ya taba jikina abunda na aikata ne shekara ashirin baya yake ta bibiyata har yau” “Nana me kika aikata?” Sai tai saurin share hawayenta ta girgiza min kai. “Ban aikata komai ba” Amsar da ta ba ni kenan ni kuma gudun an dame ta yasa ban sake cewa komai ba.Tashi nai na fito daga dakin na koma can gefen bq din na zauna ina ta tunanin maganar Nana lalai akwai abunda take boyewa kuma abunda ta aikata mai girma ne shiyasa bata son fada bata ma tana min zancen family ta ba, kuma bata taba cewa zata tafi ganin su ba ko kuma ma ta koma gida gaba daya duk kuwa da irin halin rayuwar da muke ciki. A cikin wannan tunanin ne motar Aliyu ta kunna kai cikin gidan, kawar da fuskata nai dan kar ya ga hawayena na noce kana kasa sai dai hakan be hana daya fito daga motar ya doso inda na ke ba. ALIYU POV. “Mi akai miki?” Ya tambaya fuskarsa ba yabo ba fallasa, sai ta kara yin kasa da kanta kamar tana kokarin boye kukanta. Rainawa yai daidai ita yana leken fuskarta. “Waya taba ki?” Banza ta masa ta kawar da fuskarta sai ya mike tsaye ya nufi cikin gidan ya barta da kanshin turarensa. Tun daga shigowarsa falon ya ga tv a kashe babu kowa a ciki ya san ba lafiya ba, domin sun saba kunna tv ko ba sa kallo su barshi a haka, kitchen ya fara lekawa domin ya fi tararda Momy a can ganin bata nan yasa ya wuce dakinta sai ya same ta zaune saman gadonta da magani a hannunta tana sha, yana ganin yanayinta gabansa ya fadi, da sauri ya karasa kusa da ita ya zauna bakin gadon. “Momy lafiya?” Momy bata iya ce masa komai ba sai Husna da ke tsaye ce ta labarta masa abunda ya faru. Cikin wani irin bacin rai Aliyu ya mike tsaye da zimmar fita sai Momy ta kirashi. “Ina za ka je?” “Momy ba a haifi dan da zai fada miki magana na kyale shi ba, idan ba shi da hankali to yau zan amsa shi” “Ban yarda ka ce masa komai ba, ban yarda wata magana marar dadi ta fitowa daga bakinka zuwa kunnen Muhseen, ban yarda ba” Dawowa yai ta zauna babu wani abu a duniyar da ya wuce bin umarni uwa ko da ko ba shi da dadi.Zaman sa da minti biyu zuwa uku Daddy ya shigo shi ma hankalinsa a tashe, domin ko kadan baya son tashin hankalin matarsa kamar yadda ita ma take gudun na shi. “Kin yi kuskuren aikata abunda kika aikata Hajiya, ba lallai ne Muhseen ya fahimce ki ba, kuma tabbas zai dauka kin yi hakan ne saboda ki hana shi ita ki aurawa Aliyu ita” Dagowa Momy tai ta kalli Daddy. “Ban san na yi kuskure ba sai a yanzu, kuma ta hanya daya ce na ke ganin zam iya gyarawa” Aliyu ya yi saurin kallonta. “Wace hanya?.... Momy karki ce dai za ki aurawa Muhseen ita? ” “Ta hanyar bata dama ta zabi wanda ta ke so tsakanin kai da Muhseen ko kuma wani ma dabam, idan kuma bata son auren zai tai ta karatu har lokacim da zata ji karatun ya gundireta” “Momy karki bata damar za bi Wallahi Ataa bata san wanda take so ba” “Aliyu.... ” Daddy ya kira sunansa yana kallona ya kada masa kai. “Tashi ka fita” Mikewa Aliyu yai ya fice yana jin cewar abunda Momy take son ta aikata be masa dadi ba. “Ta wannan hanyar ce kawai na ke jin cewar zan yi ma Ataa da mahaifiyarta adalci kuma na wanke kaina a gurin Muhseen, so babu abunda ba ya sakawa, idonsa ne ya rufe har ya iya fada min ba dadi kuma ya aikata abunda ya aikata, amman ba halinsa ba ne” “Amman ko ma minene ai be dace yai miki abunda yai ba, tun da ba karamin yaro ba ne shi” Husna ta fada, sai Momy ta kalli Daddy da idonta dake cike da kwallah ta ce. “Ina son ka min izini, na tafi Abuja gobe kamar yadda muka tsara, idan ma babu jirgi zan iya zaman mota” “Zuwan ki Abuja yanzu ba shi da fa'ida, zai kara lalata abun ne kawai” “Murna kawai zan tafi saboda na fadawa Fulani zan zo gobe nai mata murna” Daddy be ce komai ba ya juya ya fice daga dakin.Daddy na fita Aliyu ya dawo dakin ya xauna a inda ya zauna dazun. “Momy kar ki yi haka dan Allah, Wallahi Ataa ba zata taba ce miki tana so na ba” “Ba kai na ke son ta ce tana so ba, wanda duk zuciyarta ta natsu da shi na ke son tace tana so, idan kana da dama gobe zamu je Abuja tare da kai, Husna ki kaiwa Daddynku abinci” Tana fadar hakan ta kwantan saman gadon saboda zazzabin da take jin yana taso mata. ATAA POV. Bayan ya wuce na tashi na shiga ciki na cire kayan jikina na saka uniform din islamiyar da hijab din na fadawa Nana cewar zan tafi makaranta sannan na fito sanye da takalmina na nufi gate na fice abuna, domin an san hanyar da ya bi da ni lokacin da zai kai ni dan haka zan iya kai kaina a kafa ma domin na saba tafiyar kafa. Ban ankara ba na ga an faka mota gabana tare da bude min ganbun motar. “Shigo” Yau ya furta ba kamar ranar da ya kasa ce min na shiga ba, ba musu na shiga na rufe motar sai na dan kalleshi kadan na dauke kai, yanayinsa na canja fuskarsa da bawa mutane tsoro da yi musu barazana ta koma kalar tausayi da damuwa. Sai da ya fara tuka motar sannan kalleni a raunane ya ce. “Momy zata ba ki zabin wanda kike so” A tsakanin tambaya da labari sai na rasa wanne yake ba ni daga ciki, tambaya yake za ta ba ni zabin? Ko kuwa fada min yake. “Ban sani ba wata kila yau ko gobe ko jibi ko anjima” Sai kuma yai shiru ya cigaba da tukinsa, ni kuwa ina ta karantar abunda yake kokarin sanar min. “Ba za ki za be ni ba saboda ba ki so na, ba za ki za bi Muhseen saboda ya bata miki rai, Kamal za ki zaba saboda kina jin cewar shine kawai mutumen da be taba yi miki komai ba” Shiru ya kara yi kamar dai dazun ba sake cewa komai ba har muka isa islamiyar, waya yai ya sanarwa da malamin zuwana sannan ya fita daga motar ya zagayo gefena ya bude min na fito, sai ya tsaya yana kallona har na shige cikin makarantar.Kamin na karasa cikin makarantar malamin jiya nan ya fito ya tarbe ni, wani ajin ya kai wanda ni kadai ce a ciki sai kuma shi da ya dawo dauke da tarin littafai ya miko min. Tambaya ya soma min inda na tsaya a karatuna abunda na ke iyawa da wanda bana iyawa, sai ya fada min cewar zai mayarda ni alifun ba'un ta yadda zai zama ina iya hada harafi da kai na karanta abu, har yana fada min wai sai na yi hakuri domin zan ga a cikin sa'anina ni kadai ce na ke wannan karatun, sam hakan be dame ni ba, domin neman ilmi ne, ilmin ma wanda zai amfane ni duniya da lahira, ban taba jin cewar na girmi karatu ko kuma karatu ya girme ni ba, a kullum fata na bayan samun lafiyar Nana na samu na yai ilmi ko da kadan ne. Bayan ya gama mim gwaje gwajen da zai min ya mayarda da ni wani dakin mai cike da dalibai wasu sa'ana wasu na girme su wansu kuma sun girme me sai dai dukansu suna da karatu gwanin sha'awa abun ke nuna cewar makaranta ba a wasa da karatu. Karfe shi da daidai aka tashe bayan an saka wata Rukaiyah ta yi mana addu'ar rufewa, haka muka jero muka fitowa daga makarantar wasu na tafe suna fira da abokan tafiyarsu wasu kuma sun koma can wani bangare suna siyen wasu abubuwan na kwalan da makulashe, sosai da sosai na jidadin zuwana makarantar sai ya tuna min da lokacin da na ke karama ina zuwa wacan ilamiyar ta Clapperto ta Khalifa. A inda na bar motar Aliyu fake da zan shiga a gurin na same ta sai dai yana cikin motar zaune kuma da alama ni yake jira. Karasa nai ina kallonsa ta cikin gilashin motar wanda ya kasance fari ba kamar na dayar motarsa ba wanda ya kasance baki, ya kwantar da kujerar motar ya kwanta jikinta ya rumgume hannayensa a kirji ya lumshe ido.Ina kwankwasa kofar motar sai yai saurin bude idonsa ya kalleni tare da miko hannunsa ya bude min motar na shigo, hannuna na kai na rufo motar sannan na maida hankalina gurin littafan da ke hannuna. Shi kuma yai ma motar key mu ka kama hanyar gida. “Ataa.. Idan Momy ta ce ki fadi wanda kike so ki ce ni kinji....?” Yayi maganar ba tare da ya kalleni ba maganar ma sai rabewa take kamar an tausar numfashinsa, ban yi mamaki abunda ya fito daga bakinsa ba domin na san Aliyu yana son Momy zai iya komai dan ya faranta mata ya saka ta farinki, Saboda ya cikawa Momy burinta, Saboda ya faranta mata rai ko da baya so na zai iya rokon nai haka domin ya san a yanzu ba zai iya cilasta ni na yi dole ba. Kamar ya san abunda na ke sakawa a rai sai naga ya faka motarsa gefen titi ya kalleni ido cikin ido ya ce. “Saboda Ina son ki....!” Waigawa nai na ga ko wata aljana ce a baya da yake gani ba ni ba, sai na ga babu kowa, to ko dai shi ma ya sha wani abun ne kamar Muhseen? Anya ma dai Aliyun ne ko waninsa. “Ni ce Ataa ce” Na fada dan na tunatar da shi idan na manya wata kila ya dauka wata ce dabam ba ni ba ko kuma Rahma. Idonsa na raurau ya ce. “Ki zargi duk abunda za ki zagar Ataa, ki fada min kalamai masu zafi da da ci irin kalaman da kika san za su taba kwakwalwata, ki tsane ni adadin tsanar da kike tunanin na cancanci samu daga gareki, amman karki zabi wani bokin rayuwa bayan ni” Da gaske kalaman nan daga bakin Aliyu suke fitowa, mutumen da baya kaunar talaka da talauci shi ne ya zaunar da ni gaban motarsa yana fada min irin maganganun nan, sam ban yarda a gaske ne ba wata kila wata gadar zanen yake kulla min idan na aureshi ya rika cin ubana kullum ko kuma wani abun ne dabam, amnan idan ba shi ba taya ma Aliyu zai ce yana so na? Taya ma zai so ni da gaske? Ina da kyau ai wata kila shiyasa na canja ra'ayi ya ji yana so na.“Ban taba jin ina son ki dan wani abu na jikinki ba” Ya fada yana girgiza min kai, ashe a fili nai maganar ban sani ba. “Suna nan da yawa wadanda suka fiki kyau da komai a duniya, amman da ke Allah ya jarrabe ni, a tsakanin jiya da shekaranjiya da yau na kasa tantance irin kaunar da na ke miki, da gaske son ki na ke Ataa amman ban sani ba sai da Momy ta dora ni a hanya, sai na gane son ki ne yake ta wahalar da ni ya hana ni sukini, ban taba jin abunda na ke aji a yanzu ba, ban taba jin cewar idan wata ta zabi wani ba ni ba zan iya shiga matsala sai a kanki Ataa, ban taba jin kishin mace ba sai a kanki Ataa, ki yarda da ni ki bani dama na bude miki duniyarki, na maye miki gurbin Abubuwan da kika rasa, zan inganta rayuwarki Ataa zan nuna miki ko wanene Aliyu, ta aurenki ne kawai zan nunawa mahaifiyarki da ke kanki wanene ni, yanzu haka bana son na hada ido da Mahaifiyarki, ki taimaka min Ataa idan Momy ta tambaye ki kira sunana, ko da ba zaki so ni ba ki taimaka min ki aureni, Wallahi ina son ki Ataa... ” Saurin bude motar nai na fita sam ban yarda Aliyu bane, idan kuma shi din ne to ba kalau yake ba, da kafa na karasa gidan na bar a gurin cikin mota zaune. Gaba daya rikewa nai tunanin ma na rasa ta ina zan fara, sai nuna kai na ke ni kadai ina tambayar kaina. “Wai ni ni fa” Nana ma ta lura da hakan har ta tambaye ni abunda yake damuna, ban boye mata komai ba domin a halin da nake ciki a yanzu ina bokatar abokin da zan fadawa damuwata. “Wanene Kamal?” Ta tambaye ni domin ban sakoshi a duniyar labarin da na bata ba wacan karon a zamana Abuja. A lokacin da na gama bata kabarinta bata ce min komai ba, bata sake tambaya wani abu ba, har aka kawo mana abincin dare muka ci muka kwanta. Washe gari kamar kullum na tashi da wuri na yi sallah ni da Nana sannan na koma na kwanta ina ta tunanin abunda ya faru jiya sai komai ya zame min kamar mafarki kamar ba gaske ba.“Amman Nana Aliyu fa.... ” “Aliyu ya aikata kwatankwacin abunda na aikata a lokacin da kaddara ta rubuta min haka, yana da zuciya mai kyau Ataa tunda har iya taimaka mana ke ki samu ilmi kiji dadi rayuwa ni kuma na samu lafiya, be yi kokarin boye abun ya rufe a gidan yan sanda kamar Asim ba, mahaifiyarsa ta kyautata mana kuma ta yi fatan ki samu rayuwar jindadi shiyasa ta nemi ki auri danta, indai har mutum mai daraja mai ji da kai da kudi kamar Aliyu zai yada kansa ya bude ba ki ya roke ki ki so shi to ko ya cancanta ki so shi Ataa, ina jin a rai shi ne mijin da nake miki rokon samu kuma nake miki fatan samu, ba zan cilasta ki ba domin ni kaina cilastawa bata min amfani ba, ina baki shawara ne a matsayi na uwa kamar yadda nawa iyayen suka shawarce ni na ki” Hawaye na sauko min maganganun Nana na ratsa ni, amman har gobe zuciyata Kamal take kauna. “Karki kalli abunda Aliyu ya aikata a matsayin cin amana, domin be zalince mu ba, fada Ataa wace ya ce zata gudu ta bar iyayenta kuma ta ce zata ga kyau? Ta yi sammani komai ya zo mata da sauki? Kaddara ce a haka na gode Allah ya abun ya zo min ta nan kawai na gode ma Allah, Ataa ina son tun ina da rai na ki samu mijin da zai aure saboda Allah uwarsa ta dauke ki kamar yarta, domin ni na san mutuwa tana zuwa gobe ko anjima, ina son kamin na tafi na san na barki a cikin jindadi da farinciki, ina tsoron kar amin azaba biyu hakkin biyewa iyayena da kuma hakkin kin zaba miki miji na gari, yarinya ce ke Ataa ba ki san komai a yanzu wanda yake miki dariya yana yaba ki shi kike daukar cewar yana sonki wanda kuma yake nuna miki illar abunda kike shi kike yana kokarin kare miki mutuncin ki shi kike dauka a matsayin makiyinki, wanda kashi saba'in cikin dari na mutanen duniya haka suke, kar duniya ta rude ki kamar yadda ta yi min a lokacin da nake da kurciya, duk wanda zai so ki dan kyauki zai iya gudunki idan kyau na ki ya guje, wanda kuma ya guje ki dan talaucinki zai iya son ki idan arziki ya same ki kuma ya sake guje miki idan talauci ya rabe ki, amman wanda zai so ki dan ya gyara rayuwarki ba dan kyau ki ba, be kuma dubi talaucin da rashin danginki ba ya so shi ya fi cancanta ki so fiye da kowa Ataa, miyasa Muhseen be duka ya roki ki so shi ba? Sai ya nemi tada hankalinki? Miyasa Kamal be biyo ki har nan ya nemi ba, sai ya zabi ya kyale ki yai wata rayuwar, idan kika samu wani anjima ya ba ki abinci da kudi yai miki dariyar fuska shi za ki ce kina so, Ataa ba ki san so ba, wani be taba zowa ya ce a sallamo masa ke ba, bara kawai kike sani mu yi baran na yau da na gobe shi kawai kika sani, yadda za a baki nera ki saffarata ki ci abinci shi kawai kika sani, hakkina ne idan babanki baya raye na baki ilmi na ciyarda na shayar da ke na nema miki magani,amman ban yi ba ban koya miki komai ba sai bara Ataa, da ban gujewa dangina ba da duk haka be faru ba, shin kin samu wanda zai fanshe ni ya baki duk wannan miyasa ba za ki karba ba?” Da yaren buzanci ta jera min komai a kwakwalwarta ta karasa tana fashewa da kuka. “Guduwa kika yi Nana?” “Ba shi da amfani, tun da babu komawa har a bada babu wannan zancen” Ta fada tana share hawayenta.Ban leka sashen Momy ba sai misali goma har da rabi na safe, a lokacin har mun karya ni da Nana sai dai daga ni har ita ba mu wani ci abincin sosai ba, na yi zaton idan na ce zan je bangaren Momy zata hana ni ne amman bata ce min komai ba har na dauki kayan da muka ci abinci na nufi part din. Amina na samu a kitchen tana kuna gas da alama abincin rana zata dora tun yanzu maimakon Momy. Na gaishe ta cikin mutunci da girmamawa ita ma ta amsa min tana murmushi. “Ina Momy” “Sun tafi Abuja” Sai na ji ba dadi da amsar da ta bani wata kila abunda ya faru ne yasa suka tafi abuja, ita da wa ma suka tafi oho. “Ita da yaya Aliyu” Amina ta karasa maganar tana maida hankalinta gurin dora girkin. Juyowa nai na dawo bq ina ta tunanin dalilin tafiyar ta su, sai dai gaskiya na ji ba dadi na rashin dalili, daga tafiyar Momy har Aliyun ma, ina shigowa dakin sai Nana ta jefo min wani zance. “Mi zai saka ki zabi Kamal? Mutumen da be tana biyowa ya nemi inda kike ba?” Na zauna kusa da ita ina murza yastun hannuna na ce. “Yana da kirki sosai Nana kuma yana so na” “Yana da kirki kamar Muhseen ko kamar Aliyu?” Na yi shiru ina nazari. “Muhseen ba shi da kirki Ataa to har zai iya tunkara a matsayina na uwarki ya fada min magana irin wannan ko da ko ya san na sani, irin wannan wata rana zai iya ci miki mutunci a gabana”MUHSEEN POV. Kamar yadda yai wacan tafiyar hakan yai wannan, domin kuwa yana baro bq ya kama hanyar Abuja cikin bacin rai be taba nadamar yin wani abu kamar yadda yai nadamar zuwa sokoto ba a yau ba, domin ba be so ba da duk wannan be faru ba da be ji wata maganar marar dadi daga Momy ba, balle har yau Ataa ta ce ta tsane shi. Ya isa Abuja cikin dare kamar wacan karon sai dai yau da 11 ya shiga gidansu tsabanin wacan zuwa da ya dira karfe ukun dare. Hango wuta a falon Mama Fulani yasa ya nufi can kai tsaye domin labarta mata abunda ya faru har lokacin ya kasa sauke fushinsa. Tura kofar falon yai ya shiga sai ya same ta zaune bakin saman kujera tana kallon tv. Karasa yai kusa da ita yana wani bata rai shi ala dole fushi yake yana kuma son nuna mata damuwar, kusa da ita ya zauna, ganin bata kalleshi ba yasa ya kira sunanta. “Mama....” Tana juyowa ta tsinka masa mari mai zafi da bayan hannunta ta mike tsaye a fusace tana kallonsa ta ce. “Sha sha sha marar tunani sakaraiz ashe Muhseen baka da hankali ban sani ba sai yau? Waya kai ka taba Momy? Wa kake a cikin Familyn mu da zaka fadawa Momy marar dadi wa ke? Da? Da? Dan da zaka iya mutuwa yau gobe na haifi wani? Ka taba kowa ka yi ma kowa amman ban da Momy ban aminta ba, ban aminta ko inuwarta ta kata ba, balle har ka fada mata ba dadi idan ka taba uwar Aliyu uwarka ka taba tashi ka fice min daga falon, daman kai nake jira dan sannan za ka zo, get out....!” Ta furta a tsawace tana nuna masa kofar fita. Hawaye shar suka wanke fuskar Muhseen tuni yai mutuwar zaune a gurin. ZAKI By Khadeeja Candy 41... Kasa cewa komai Muhseen yai sai kallon Mama Fulani yake hawaye na sauko masa kamar ba shi ba. A fusace ta bar masa gurin ta haye sama dakinta. Ya dade zaune a gurin sannan ya mike tsaye ya nufi part dinsa, keys bude dakin ma daker ya iya sakawa ya bude yana shiga ya zube a falo zaune saman kananan cushion dinsa. Abunda ya faru ne ya tsaya masa a rai, ta ina ne be kyautawa Momy ba? Miye illar abunda yai? Har ga Allah be ga da inda yake da wata matsala ba, Momy ta nuna masa son kai, kuma maganar da ya fada mata babu laifi a ciki, ta sani sarai yana son Ataa taya zata juyar abun akan Aliyu saboda yana danta? Ya sani be kyautawa Ataa na fada mata maganar kai tsaye a gaban mahaifiyarta ba, sai dai be san cewa mahaifiyarta bata sani ba da be aikata abunda ya aikata har ta furta kalmar tsana a gareshi ba, wannan babin kam ya yarda yayi kuskure amman da wanne zai ji rashin goyon bayan Momy ko kuwa yanke masa hukunci da mari da Mama Fulani tai, ko kuwa auren Ataa da Aliyu zai yi? Anya ma zai iya zai iya kallon Ataa da Aliyu a guri daya bayan shi ya fi cancanta ya zauna da ita? Domin shi ya ce yana son ta kuma yana da tabbacin tana son sa. A daren be yi bachi ba duk kuwa da irin gajiyar da ke tattare da shi na tafiya mota amman tunani ya hana shi bachi kamar wacan karo, ta ina yake da matsala ina zai samu mafita? Ta ina zai shirya da Ataa? It's necessary ya koma sokoto ko gobe? Asubar fari ya fita daga gidan zuwa masallaci be dawo ba sai takwas da wani abu na safe, kamar zai wuce part dinsa sai kuka ya shigo part din Mama Fulani ita ya samu tana share falon da kanta Maryam da Rukaiya na zaune sai aikin danna waya suke. “Mama ina kwana?” Ta yi kamar ba ta ji shi ba sai cigaba tai da aikinta. “Mama Muhseen na gaisheshe ki” Maryam ta fada a zatonta bata ji abunda Muhseen yace ba ne. “Na ji ai” Ta fada ba tare da ta kalleshi ba. Shi kuma ya mike tsaye cikin rashin jindadi ya fice daga falon.“Gaskiya Mama be kamata ki ga laifin Ya Muhseen ba, har ga Allah Momy be kamata tai supporting Ya Aliyu ta bar Ya Muhseen ba” Mama Fulani ta dago tana kallon Maryam wacce tai maganar tana nuna ta da tsintsiya. “Baki san komai a kan rayuwar yara ba, babu ruwanki a ciki duk wanda zai ce kushe min Momy zai yi to zai jawa kansa bakin jini ne kawai, ai Aliyu ya fi cancantar karin aure yanzu fiye da Muhseen ko dan saboda Rahma, sannan Momy mai zaba masu matar aure ne, waya sani ko ta zaba masa wata ne shi Muhseen din ya ce baya so sai ta Aliyu, ai Amina ta fada min mafarin fadan duk akan wata yarinya ne” “Haka ne kuma, su ma dai ban da abun su miye abun fada kan mace ga mata nan da yawa a gari, dama Ya Aliyu ya bar masa ko wacece ya zo ya auri Rukaiya” “ai na ga kamar bata masa ne shiyasa ban matsa ba bana son abunda zai jawa Aliyu matsala, kuma namiji kara dai ka jira har kawo maka wacce yake so da wacce kai kake so, kin san dai duk yarinyar da Aliyu zai so classic lady ce, ai ko dan ya ba wa wannan yar iskar Rahma haushi zan zo ya aure ta” Rukaiya ta yi kunce tana danna wayarta ta ce “Uhmm ni jikina na ba ni Ataa ce suke wannan rigimar akanta Wallahi, kin san fa tun tana gidan nan suka fara wani zafi zafi akanta” Mama Fulani ta dan yi shiru kamin ta kalli Rukaiyah. “Ai ko kowa zai yi ban da Aliyu, ai sam ba zai taba son wannan banlagarar yarinyar ba” “Mama tana da kyau fa sosai, kuma nan zai iya rudarsu, shi dai Ya Muhseen tun da a nan ai ya furta” “Ai yau Momyn zata zo za mu idan ita ce din, amman ni nasan Aliyu ba zai taba son irin wannan yarinyar ba” “Uhm Mama ba ki sani ba kenan, ai Wallahi Ya Aliyu zai iya jin cewar zai gyarata ya zauna da ita” “Yarinyar da ke bara a titi dan Allah ki bar ma wannan maganar bakinki ya sari danyen kashi amman dai ba akan yayana ba Wallahi” Mama Fulani ta karasa tana tofarda yawu, a take ranta ya bace domin ko maganar Ataa bata son a mata a yanzu sam ta ma manta da ita a duniyarta.Misalin goma na safe Momy da Aliyu suka sauka Abuja, suna sauka yai ma Nasir waya ya zo da mota ya dauke su zuwa gidan Mama Fulani, a motar ne Nasir yake karantar damuwar Aliyu domim tsakanin jiya zuwa yau har wata rama yai idonsa sun dan fada kana ganinsa kasan akwai damuwa a tare da shi, sai dai fuskarsa na nan a daure kamar ko yaushe. Suna isa gida Aliyu ya fara bude motar ya zai fita sai Nasir ya hana shi ta hanyar ce masa. “Aliyu ina son mu yi magana da kai” Jim hakan yasa shi zaunawa a motar Momy kuma ta bude gidan baya ta fita zuwa cikin gidan sai da ta shige sannan Nasir ya kalli Aliyu ya ce. “Wani abun ne kuma ya sake faruwa?” “Babu komai Nasir” “Ga fuskarka nan ta nuna damuwa” “Ina jin zaman jirgi ne” “Zaman jirgi daga sokoto zuwa Abuja zai saka cikin damuwa” “Babu wata damuwa a tare da ni Nasir kai ne kake ganin haka” Yana fadar hakan ya fice daga motar zuwa cikin gidan, yana jin cewar matsalarsa da Rahma private matsala ne da ba lallai sai aminnsa ya ji irin zaman da suke ba, matsalarsa da Muhseen ma yana jin ta su ce ta cikin gida da wani be kamata ya ji ba, balle kuma na son Ataa daya hana shi walwala wata kila ma idan ya fada masa dariya zai masa. Ko da ya shiga Momy na falo zaune ita da Mama Fulani ta jera mata fruits domin abincin rana be kai ba kuma bata jin zasu fito ba su karya ba. Kusa da Mama Fulani Aliyu ya zauna yana murmushi karfin hali. “Mama ba ki fada min maganar Kamfanin nan ba sai a gurin Momy na ji” “Ai da gangan na ki fada maka, wai ka tashi ta wuce sokoto ta waya ma kake fada min cewar ka wuce sokoto kai mai mata duk inda take kafarka na nan” Dariya yai ya ahafa kansa yana kallon Maryam da Rukaiya da suka dauko kular farfesu Maryam kuma ta dauko plates da spoons. Maryam ce ta fara gaishe shi kamin Rukaiya ta dora da nata sai ya amsa musu fuska a hade kamar yadda ya saba.“Oh to sai na zuba masa ido yai miki rashin kunya kuma na kyale shi? Dan kin zaba masa mata ma ya isa ya ce ba zai aureta ba balle kuma dan kin zabawa Aliyu ita, yau ba ni burin da ya wuce na Aliyu ya kara aure” “Wannan dalilin ne yasa na so Aliyu ya aureta amman ai Muhseen ya kasa fahimtata, kwana biyu da suka wuce Rahma dai fushi...... ” Momy ta labartawa Mama Fulani abunda ya faru ciki har da jawabin da Mahaifiyar Rahma tai mata, a take ran Mama Fulani ya bace “Uban me suke takama da shi a duniyar nan? Su har suna da bakin yi ma mutane iskanci? Ai shiyasa na ke son ya kara aure mu nunawa amaryar kauna in yaso ita sai ta mutu, ya yana bukatar aure ko Allah zai ba shi haihuwa ma, ta san da maganar auren ne? Amman zan cen ba aza ayi kishi da talaka ba kam tana da gaskiyarta wa yake son rabar talaka” Momy ta hade yawun bakinta kana ta ce. “Bata sani ba, yanzu haka tana dubai taje hutu” “Ahhh hutu ko? Aiko kamin ta dawo za ayi auren nan, idan ma ni Aliyu zai dauki shawarata ya aika mata da saki kawai ni fa bana son rai ni” “Ba sai ya sake ta ba, kin san halinndan ki ai ba lallai ne ya ce zai yarda ya sake ta ba, amman ko auren ya kara ai sai samu saukinta, amman yanzu ni na janye maganar auren ma kara dai ta zaba tsakanin shi da Muhseen duk wanda take kauna sai a aura mata shi idan ma wani take so ba shi ba sai a aura mata?” “Wacece wai?” “Ataa” “Ataa” Mama Fulani ta maimaita tana kallon Momy baki sake. “Kam uban nan” Ta daki kirji ta buga kafa da kasa. “Dan Allah idan wasa kike ma ki daina” “Babu zancen wasa a ciki Wallahi gaskiya na ke fada miki, Ataa ce” “Ataa dai wacce tai aiki a karkashinmu? Ita ta samu wannan damar da har Muhseen da Aliyu suke ribibinta ko kuwa dai wata Ataa dabam, yar aikin gidansu? Yar talakawa yar bara a titi? Dan kari, ita ce kike cewa za ki bata dama ta zaba? Har kike tunanin bata Aliyu? Ko dai kin manta wacece ita?”“Miye abun mantuwa a ciki? Yarinyar da a hannuna ta ke yanzu, talauci ba illa ba ne” “Aa Wallahi illa ne idan kina da talaucin anya kina ganin za ki iya shiga jirgi ki zo Abuja yau? Na dauka yar wata manyan mutane ce a cikin sokoto ko nigeria ma” “A haka dai yayanki suke sonta” “Lalala ban yarda ba, ina dalilin jayaya akan wannan banzar yarinyar? To ko dai ta shanye ku ne gaba daya? Daman ance buzayen nan mayu ne, ke kira min Aliyu yanzu nan” Mama Fulani ta karasa tana kallon Rukaiya a take Rukaiya ta kira a waya ta sanar masa Mama Fulani na son ganinsa, daman yana garden yana ta kallon gurin da Ataa ta saba tsayawa ta wanke plate dinta gani yake kamar tana a gurin. Be bata lokaci ba ya shigo falon. “Aliyu Ataa kake so? Ko kuwa Momy ce take son taka maka ita ta cilasta maka?” Tun kan ya karaso kusa da ita ta aika masa da wannan tambayar. Sai dai be amsa mata ba sai da ya karaso kusa da ita ya zauna. “Mama na yi wani abun ne?” “Wa kake so? Wa kake son ka kara aura a matsayin mata ta biyu?” “Ataa Mama and i need your support” “My support? Aliyu are you out of your Sense? Yar talakawan yar aikin gidanku” Yayi shiru be ce komai ba. “Lalala ban aminta ba ka cireta a ranka tun wuri, eyy yarinya ta samu matsayi har da wani bata zabi ake tsakanin Aliyu da Muhseen ko? Eh lallai” Daga Aliyu har Momy shiru sukai, Momy bata son saka bakinta saboda Aliyu ne, shi kuma ya rasa kalmomin da zai hada ya fahimtar da Mama Fulani ta ya ma za'ayi ta fahimta, yasan duk wanda zai fadawa yana son Ataa a yanzu zai yi mamaki. Fada sosai Mama Fulani ta fara masa ta inda take shiga ba ta nan take fita ba, tun yana iya saurare har ya ji kunnuwansa ba za su iya daukar yadda take aibanta Ataa ba a gabansa. Harabar gidan ya fito yana sacikawa bakinsa iska ya busar.Part din Ammy ya nufa daman bata san da zuwansu ba, domin Momy ba ta kira ta fada mata tana nan zuwa kamar yadda ta saba ba. Ta yi farinciki sosai da ganinsa daman ita kadai ce a falon. Ba laifin ya dan sake yayi fira da ita duk kuwa da be saba hakan ba domin zancensa be eh a a ba, sai kuma tambayar wani abu idan ta kama.    Fried rice da miya ta kawo masa ya karba ba dan yana jin yana son ci ba, domin ko da safe da Lipton kawai ya karya be sake cin komai ba. Wayarsa ce tai ringing yana dubawa ya ga Number Abbah, yayi mamakin ganin kiransa domin ba kasafai yake kiransa ba sai idan wani abun ya taso. “Assalamu Alaikum Abbah” “Wa'alaikassalam, Aliyu kun shigo abujar ne?” “Eh Abbah” “Ka same ni office yanzu” “Okay Abbah” Yana sauke wayar ya aje plate din abincin ya mike tsaye. “Ammy Abbah yana nema na bari na je na dawo” “To a dawo lafiya abincin sai ka dawo ko” “Eh” Ya fice da sauri cike da son sanin dalilin kiran da Abbah yake masa. Sai da ya shiga part dinsa ya dauki keys din motarsa da ke gidan,sannan ya fito ya bude motar ya shiga. Cikin ka kannen lokaci ya isa kamfanin kamin ya isa office dinsa ya kira a waya ya sanar masa ga shi nan zuwa, sai Abbah ya ce ya jira shi office din yana wani gurin meeting a kamfani, haka Aliyu ya shiga ya zauna har aka kira sallah Azahar ya fita yaje yai sallah ya dawo ya zauna a ciki yana jiran Abbah. Sai kusam uku da yan mintuna Abbah ya shigo office din rike da takardu a hannunsa. Cikinnl girmamawa Aliyu ya gaishe shi ya sama masa yana murmushi sannan ya zauna a kujerarsa mai lilo yana kallon Aliyu ya ce. “Hajiya Fulani fada abunda ya faru” Aliyu ya yi kamar be san komai ba. “Na me Abbah?” “Ance Momy ta zaba muku mata kai da Muhseen ko? Shi Muhseen ya ki yarda ya ce ta ka yake so?” Aliyu ya yi kasa da kansa. “Na kira Daddynku na yi magana da shi, indai yarinya tana son ka kana son ta za a aura maka ita” Da sauri Aliyu ya kalli Abbah, sai ya rasa abunda zai ce, sam be tsammaci haka daga gurin Abbah ba. “Amman Abbah Mama bata so, saboda yarinyar ba yar masu kudi ba ce, tana ganin kamar kaskanci ne a gurina da gurinta?” “Yarinyar bata da tarbiya ne?” “Tana da Abbah talauci ne kawai matsalarta” “Kar wannan ya dame ka idan ka ce zaka biye fulani da tsare tsarenta zaka sha wahala kamin ka samu wacce zata dace da ra'ayinta”“Abbah idan bata so zai zama da matsala a ciki, yanzu haka fadan da ta gama min kenan?” “Kai iyayen yarinyar sun tashi aurar da ita? Kuma ka tabbatar tana son ka?” “Momy ce zata mata komai, kuma ba dole ne idan a daura ta tare a lokacin ba, amman daurawar zai kwantar min da hankali Abbah” “To ka shirya assabar mai zuwa za a daura muku aure” “Abbah da gaske?” “Na taba maka wasa? Ka shirya kuma ka sanar da iyeyenta ka sadani da su ni nan zan daura maka aure” “Abbah....” Sai kuma yai shiru Abbah ya kalleshi da kyau. “Wani abun ne?” “Gaskiyar yarinyar bata kowa a yanzu, daman yan nijar ne kuma mahaifinta ya rasu ba su koma ba, mahaifiyarta ce kawai a raye yanzu haka a gidan Momy take zaune saboda yana ba su da inda za su raba” “To yanzu ya kake son yi? Ba wata matsala Abbah wannan ce kawai” “Za a san yadda za ayi, Daddyn ma ya ce zai tambayi yarinyar idan tana son ka In-Sha-Allah za a aura maka ita kar maganar Haj Fulani ya tashi hankalinka” Gaban Aliyu ya fadi jin cewar za a tambayi Ataa idan tana sonshi sai dai hakan be hana shi murna ba har da zagayawa ta inda Abbah yake yai masa godiya sannan ya taso ya fito office din ransa fari tas. Be taba jindadin zuwansa abuja kamar na yau ba, ganin yake wannan zuwan ya fi ko wane saka shi farinciki da jindadi fiye da ko wane. Haka ya isa gida da farinciki kamar wanda aka yi ma kyauta karin rayuwa. Sam ba zaka ganshi yanzu ka ce shine ya fita dazun a haka ba, yanzu kan kana ganinsa ka san yana cikin farinciki. A daki ya samu Momy da Mama Fulani sai kuma Muhseen da ke zaune gefen Mama Fulani kansa a kasa da alama hakuri yake bawa Momy. “In banda abinku yanzu wannan yarinyar ce har zata shiga tsakaninku? Wallahi Ni abun har mamaki yake ba ni, abu kamar a shirin film wai kuna son yarinyar nan har da kai Aliyu, duk matan duniyar nan? ” Aliyu ya nemi guri saman kujera ya zauna yana shiga da fitarda numfashinsa a hankali. “Na sani Momy ta isa ta zaba min mata, a lokacin da Momy tai min maganar nan raina ne ya bace sosai har na kasa controlling kaina, amman Mama ta nuna min illar abunda nai Abbah ma haka, Momy ina neman yafiyar dan Allah ki yi hakuri” “Ba komai Wallahi ya wuce a gurina, taya ma zan ga laifinka? Abunda nai kana fa gaskiya yayi kama da son kai, kuma be da ce na yi haka ba” “Haka shine daidai Momy, ban cancanci zama..... ” Na dauki lokaci kamin ya karasa ragowar kalamar.“Zama... Mijin... Ataa... Ba... Sai dai har gobe ban yarda akwai wani hali nawa da zai iya hana ni auren Ataa ba... Kuma zan hakura da ita saboda kawai na zama mai biyayya a gareku kuma ba zan sake yin maganar ta ba, amman tana nan a zuciyata” Jikin Momy ne kawai yai sanyi yayinda Aliyu kuma ya shiga wani tunanin yana ganin kamar Muhseen ba zai hakura haka nan kawai ba, wata kila ya canja shawara ne ko kuma yana shirin bullo da wani abun, amman wannan duk mai sauki ne idan har ya samu ya auri Ataa duk wani abun da zai biyo baya mai sauki ne a gareshi, and it would be better if be fadawa kowa zancen da su ka yi da Abbah ba, har sai idan a tsakaninsu maganar ta fito. “Babu rashin cancanta a aurenka da Ataa, saboda son aure kake mata kuma zaka auri Ataa matukar ta bude baki ta furta cewar kai take so” Mama Fulani ta tari numfashin Momy tana daga mata hannun. “Saboda girman Allah ki daina wannan maganar ma, wani irin ta zaba sai ka ce wasu awaki ko gwanjo? Muhseen dai ya gane kuskurensa kuma ya dawo a hanya, Allah ya raba su da wahala amman yarinya ta zame mana bala'i” Har cikin ransa Aliyu ya ji kalmar bala'i da ta kira Ataa da ita har sai da yaja numfashi ta sauke. “Na hakuri da Ataa Momy ina mata fatan miji na gari, and zancen Amina ina son a bani kwana biyu zan yi shawara” Momy ta gyada masa kai idonta na cika da kwalla zuciyarsa na raya mata bata tai daidai ba, kuma bata kyautawa Muhseen ba. Mikewa yai tsaye jiki a sanyaye ua fito daga dakin da ya sauko kasa sai da ya saka hannunsa ya dafa zuciyarsa ya daga kansa sama ya hade yawu sannan ya cigaba da sauka stairs din.Aliyu ma tashi yai ya fice daga dakin zuwa cikin motarsa, wayarsa ya ciro ya kira Husna ringing biyu ta daga tana kiran sunansa. “Husna ki je bq idan Ataa na nan ki kira ta gefe ki bata waya” “Tau” Bata kashe wayarba domin ta san halin yayanta baya son a kashe masa waya, yana jin lokacin da tai sallama ta shiga ta gaishe da Nana ta tambayi Ataa Nana ta ce masa ta tafi makaranta, sai dai bata amsa masa ba sai da ta fito daga bq sannan ta kara wayar a kunnenta. “Yaya bata nan wai ta tafi islamiya” Be ce komai ba ya kashe wayar zuciyarsa na raya masa wani zai tare ta a hanya yai mata magana ko ya yaba kyauta.gaba daya yanzu hankalinsa ya koma gurin Ataa ya manata da kowa da komai da ke gabansa. ATAA POV. karfe shida muka taso daga ilslamiyar kamar dai jiya, maganganun Nana na ta min yawo a kwakwalwa ga kuma tunanin abunda ya baro ta da familynta ya tsaya min a rai, guduwa dai ta alama amman miye silar gudurwar da har take ganin abunda aka aikata mata sakamako ne a gurinta? Ga kuma maganar Aliyu ma ta tsaya min a rai ashe zai iya zubar da kansa kamar haka ya furta min kalamai irin wadannan? Haka nan kawai na ji ina da bukatar ganin fuskarsa wata kila dan na kara tabbatarwa ne ko kuwa dan jiya ne abun ya faru na ke son sake faruwarsa a yau duka ba zan iya yanke hukunci ba a yanzu. “Assalamu Alaikum” Wata kyakkawar muryar mai dadi sauraro ta yi min sallama ta bayana, sai na juyo na ina amsawa tare da kallon mai sallamar. Bakin mutum ne cikin shadda ruwan kasa da hularsa mai haske taba ni ka ji hadisi sajensa ya kwanta gwanin sha'awa kama ganinsa ka san irin ustazan nan ne da ko kallon mata basa son yi. “Dan Allah ina ne gidanku?” “Lafiya?” “Lafiya Kalau nuna min kawai na ke son ki yi” “Can mai jan gate” Da hannu na nuna masa kasancewar ina daf da gidan ne. “Na gode” Sai kawai yai gaba ya bar ni a gurin tsaye da mamaki, da kallo na bishi har sai da na daina hango shi sannan na karasa gate din na buga aka bude min na shiga ciki, harabar gidan na ke hangowa ina son tantance abunda na ke hangowa Doc Bukar ne tsaye da Daddy suna gaisawa, har na yi kamar ban gansu ba zan wuce sai Doc Bukar ya kira ni. “Aisha....” “Na'am” Na amsa sannan na juyo na doso inda yake tsaye, har kasa na risina na gaishe da Daddy ya amsa min da far'a yana nufi kofar falon ya bar ni da Doc Bukar tsaye muna gaisawa. “Daman na zo gurin Aliyu ne kuma ba ya ne sai ga Daddy ya shigo muka gaisa” Na yi shiru ban ce komai ba sai gyra littafaina na ke hannuna. “Daman kullum ina son na zo mu gaisa sai Aliyu ya ce ba ki gidan, ya mai jiki?” “Al-hamdulillah” Ganin ina masa ciki ciki kuma babu sakewa a tare da ni ya saka ya bude motarsa ya dauko kudi ya miko min. “Gashi ki gaida Mama” Kasa Karba nai, daman ko lokacin da nake bara ina neman kudi dalili ne wanda a yanzu babu shi. “Aa na gode” Na juya na nufi bq din na bar shi a gurin tsaye, sai da na shiga na cire uniform dina na saka wata doguwar riga sannan na ji tashin motarsa a lokacin Nana ta fito daga bandaki. “Kin dawo” “Eh Nana ya jikin na ki?” “Al-hamdulillah, Hajiya ta dawo?” “A a wani abun ne?” “Idan ta dawo ki sanar da ni, ya kamata mu tafi wani gurin kuma tun kamin mu saba da nan” “Wani gurin zamu je kuma Nana?” “Eh In-Sha-Allah” “Amman miyasa?” Bata ba ni amsa ba Siyama tai sallama ta shigo wai na zo Daddy yana nemana, Hijab dina na dauka na saka na bi bayanta jin kiran Daddy da kansa na sam abu ne mai muhimmanci, har part dinsa ta shiga da ni yana zaune kasan carpet da kofin ruwa a gabansa da waya har biyu yana dannawa. Ko a. Lokacim da ya amsa min sallamata bw kalle ni ba ya amsa min ne kawai sai Siyama ta mike ta fita ta barni. Kaina a kasa lokacin daya aje wayar ya soma min magana. “Abunda ya faru ya riga ya faru ki manta da komai kuma ki dauka komai be faru ba, mu tamkar ya muka dauke ki dan haka za mu iya yi miki komai kamar yar da muka haifa, ki janye maganar Momy ko ta Muhseen ko ta Aliyu, na ba ki kwana biyu ki je ki yi tunani ki fada mana wanda kike so, sati mai zuwa auren kuma ba zai hana ki karatu ba za a miki auren ne saboda ki samu natsuwa kowa ma ya samu, Momy za tai maganar da Mahaifiyarki idan ta dawo gobe wannan tsakanina da ke ne” Sati daya? Kamar wata yar tsana? Kamar ua sati daya? Sum gaji da mu ne ko kuwa dai suna son tsawwalawa mana ne ko kuma wani abun ne da dabam.da wannan tunanin na taso na dawo bq kaina a kulle. ZAKI By Khadeeja Candy 42... A daki na samu Nana zaune ta rafka tagumi tana kallon kofa kamar mai jiran shigowata. Nima damuwar ce a fuskata na maganar da Dddy ya fada min yanzu, sai dai na yi kokarin moye tawa damuwar tare da tambayar abunda yake damunta da kuma dalilin barin gidan da take son mu yi bayan na fara karatu a yanzu abunda na rasa shekaru da dama. “Nana miyasa kike son mu tafi? Momy ta roke ki da mu zauna kuma karatun da na fara dainawa zan yi Nana idan muka tafi” Hawaye na gani a fuskarta. “Ina ganin kamar zaman gidan nan matsala a gurin na ina ganin kamar son ki ya haddasa wata kiyayya ko kuma fada a tsakanin yan'uwa biyu, Hajiyar gidan nan ta mana karamci iya karanci ba kowa zai yarda ya zauna da irin mu ba, amman ta zauna da mu ta nuna mana kauna, ban san miye alakar Muhseen da Aliyu ba, na san dai yan'uwane amman yan'uwanta kan da ina ne ban sani ba, bana son na zama silar rushewar wasu iyalin bayan barin nawa da nai” “Nana miyasa kika yi wannan maganar?” “Na baki shawara auren Aliyu ne a mahangar da na ke ganin ta dace da ke kuma na ke ganin kamar ba zata cutar da ke ba, na san ba ki san so na kuma ba lallai ne ki iya fahimtar komai a yanzu ba wata kila sai gaba, kina da damar zaben wanda kike ganin ya dace da ke Ataa kuma wanda kike jin ya kwanta miki a rai” “Miyasa kika ce haka?” “Sayan tafiyarki islamiya, Husna ta shigo da waya tana neman na fada mata ta kin tafi makaranta, an jima kadan kuma sai Amina ta zo wayar ta miko min wai Muhseen yana son magana da ni, hakuri ya fara bani sannan ya fada min cewar ya hakura duk abunda zai raba kan Mahaifiyarsa da Mahaifiyar Aliyu zai iya hakura da shi, duk kuma abunda zai iya shiga tsakanin mahaifinsa da mahaifin Aliyu zai iya hakura da shi, ya fada min idan kika aureshi ba ki auri Aliyu ba, Aliyu da iyayensa za su ga cewar ba ki kyauta musu ba kuma ba mu musu karamci ba, idan kuma kika auri Aliyu kika barshi zai hakura amman ba zai taba iya cire son ki a ransa ba, kuma yasa iyayensa ba za au daina ganin cewar iyayen Aliyu sun yi son kai ba, ya ba ni hakuri ya fada min akwai zumuncin mai karfi a tsakaninsu, kar na bari zumincinsu ya lalace” Na dan yi shiru ina tunanin wata kila tsoron lalacewar zumincin ne ya saka Momy ta tafi Abuja, ko da yake daman na san tana da ra'ayin zuwa tun a wacan karon da tai min albishirin zuwa da ni. “Amman Nana wannan abun ya isa ya saka ki ce mu bar gidan nan? Idan muka tafi ina zamu zauna? Babu mai karbar mu sai yawon rabe rabe a titi, haka rayuwar mu zata kare? Ba kowa a tare da mu kuma sai mun yi ba ra mu ci? Kullum wani kalar kabulen muke fuskanta? Indan har za mu bar nan kamata yai ace cikin danginmu za mu koma, Nana ban san kowa na ki ba, ban san kowa na mahaifina ba, miyasa kika gudu kika dawo nan kin kasa fada min kullum sai boyewa kike bayan nima ina da hakkin sani domin ni yarki ce” “Ba dadi ne ya rabo ni da iyayema ba, shiyasa ba zan iya koma musu ba, na musu tuluci sai kuma yanzu na ce zan koma? Ai abun ma da kunya” “Mi kika aikata Nana? Butulcin me kika musu?” Shiru tai na wani lokaci tana hawaye. “Na yi ma iyayena budulci, kuma na gudu na barsu ina jin kunyar komawa a yanzu ina jin kunyar arba da mahaifina da mahaifiyata waya sani ko su yi min mummanar kalami bayan tafiyata” “Mi kika yi har ya koreki?” “Ba korata yai ba guduwa nai a karan kaina” “Saboda mi nana?” “Saboda Soyayar mahaifinki, na so mahaifinki kamar na mutu ina ta ganin kamar idan zan yi rayuwa ba da shi ba zan iya mutuwa ko na fada halaka, a Masarautar mu mace ba ta zabawa kanta mijin aure sa dai iyaye su zaba mata, ni kuma nai kuskuren zaba da kaina kuma a ganina ba laifina ba ne idan na zabawa kaina mijin da ya fi kwantar min a rai” “Masautarku kike ce Nana? Kin saka kaina a cikin duhu ban gane ba” “Ba zaki gane ba Ataa ba lallai ne kowa ya yarda ba balle har a iya tsayawa a gane, kowa yana ganina a wulakance a kaskance amman ni jinin sarauta ce ni kadai ce ya mace a gurin Sarki Bashiru Muhammadu, ni kadai ce Gimbiya Nana Asma'u a duk fadin masarautar Agadez” Ba zan na kasa yarda da abunda Nana take fada min ba, amman tabbas labarin nan abun rikitarwa ne. “Amman Nana muka kare a bara?” Na tambaya cike da zakuwar son jin labarinta. Numfasawa gai sannan ta ce “ Yankin Agadez shi ne ya fi kowanne yanki girma a Nijar, yankin Agadez ya hada da hamadar Tenere da Bilma da kuma yankin Air mai cike da tsaunuka. Mafi yawancin jama'ar yankin Abzinawa ne, akwai kuma Tubawa da Fulani da kuma Hausawa, mahaifina shine sarkin Agadaz, babban sarki ne mai tari dukiya da kaddarori da mu kan mu yayansa ba za mu iya fayyace ta a lokaci daya ba, mu goma shar tara mahaifinmu ya haifa a dakinmu mu bakwai ne, mahaifiyarmu ita ce uwargida, bayan ita yana da mata biyu, amman ni kadai Allah ya ba shi mace duka sauran maza ne, na taso a cikin wani irin gata marar misaltuwa, kasancewa ta mace sai ya zama ta ko wane bangare ina samun kulawa, bangaren Mai martaba ba, yayyuna maza har ma da kanena maza idan wani abun burgewa na mata suka gani sai su siyo min, domin ni ban san taso a gidanmu na san wani wai kiyaya ki yan ubanci ba, dukanmu idan ka ganmu zaka dauka uwa ta haife mu, boyona ake bana fita ko'ina sai idan makaranta ne ko wani muhimmin abu, karatun addinin ma malami aka samo a gida yake koya mana komai, a lokacin da na gama karatu matakin na biyu, sai mahaifina ya kai ni faransa domin ci gaba da karatuna, a lokacin ban iya komai ba sai faransanci da buzanci a wacan lokacin, ina dawowa a duk lokacin da hutu ya samu sai dai na kan yi watanni kamin na dawo gida, a wata dawowa da nai sai na samu masarautar mu ta yi sabin gyare gyare cikin har da daukar sababin ma'aikata mahaifinki na daga cikin ma'aikatan da aka dauka, ranar da na sauka masarautar mu mahaifinki ne ya bude min mota” Ta yi shiru na wani lokaci sanna ta cigaba. “Yana kyau sosai kamar ki, tun a farkon ganin da nai masa na ni ya kwanta min a rai, duk kuwa da kasancewar ban san soyayya ba, saboda mahaifina baya bari wani namjin ya rabe, saboda mazan gidan ma ma zabin mata ake musu balle kuma mata, amman a lokacin da na ga mahaifinki sai ya shiga raina sosai na kamu da son shi, ba kasafai na ke fitowa a harabar masarautar mu ba, amman zuwan mahaifinki sai na fito na zauna nai ta kallonsa ko kuma na kuma na rika lekensa, ina yin duk wani abu da zai kusantar da ni a gareshi, idan lokacin zuwansa yai be zo na duk sai na bi na damu, har wata na shirya fita ta musamman zuwa gidan gonar Mai Martaba da sunan shakatawa, ni da kaina na zabi wadanda za su raka ni, a ciki na za bi mahaifinki, mutumen ne mai far'a da son mutane, sai dai yana tsoron ko da kallona yai kasacewata yar saurata, sai dai na yi da jansa a jikina ina nuna masa kauna, ya labarta min yan'uwana da kowa na sa da ke garin Agadez, wasa wasa kauna ta shiga tsakaminmu amman a boye bana bari a sani,  ina daf da komawa makaranta Mai martaba ya gabatar min da wani dan aminsa atsayin mijin da zan aura idan na kammala karatuna, a lokacin ne na juyawa Mai martaba baya na fada masa kai tsaye cewar mahaifinki ne so, a lokacin ne mai martaba ya cilasta ni kula dan aminsa, mahaifinki kuma aka koreshi daga masarautar, babu yadda mahaifiyata ba tai ba dan ta fahimtar ta shi amman ya ki fahimta, aka cilasta min komawa makaranta a cikin wannan yanayin, na shiga damuwa matuka ina jin cewar da zarar na sakw dawowa a garin mai martaba zai aura min wani ne dabam na ummaruje ba, daga makarantar na dawo nijar ba tare da sanin mai martaba ba, na sauka a wani hotel na chanja shigata nai shigar da ba za a taba iya gane ni ba, na je da kaina har cikin gidan su Ummaruje, tsoro sai ya kama mahaifiyarsa da mahaifinsa da dukan yan gidan kasacewar gidan yawa ne, suna ganin cewar idan mai martaba ya san na zo nan zai iya fusace yai musu wani abun, ni na fada masa durina na guduwa, kuma ya yarda saboda so na sosai daga Agadez muka yi doso gurin wasu yan'uwansa, suma suna ya jin tsoro daker muka samu suka yarda aka daura mana aure a sirrance, sai labarin neman Ummaruje ya fara karade nijar, muka sake guduwa da dan abunda yake hannuna muka dawo kamba, da kudin hannuna muka kama haya, mahaifinki kuma hai shago kofar gida, kuma sai Allah yasa albarka abun ya karbu, sai da na shekara biyar a kamba sannan na haife ki, daga nan sai mutane suka fara tambayar dangina, ganin kowa be zo sunanki ba daga dangin mijina har nawa, daga haka muka fara jin mutane umguwa na zancen wai ni yar sarki ce, sai zaman ya gagare mu a nan saboda tsoro da fargaban abunda zai biyo baya, muna ta ganin kamar Mai martaba zai iya aikowa nemana ko kuma ya saka a kama Ummaruje, ya siyarda komai nasa kudin hayar mu kuma muka barsu nan muka koma argungu, zaman a can be karbe mu ba saboda sanar'a shagon da mahaifinki ya fara yi sai ta soma komawa shiririta, sai muka bar yankin gaba daya muka shiga bodinga, a lokacin ne mahaifinki ya fara sana'ar tura ruwa yana siyarwa, sai dai zaman kaune babu dadi saboda ban saba ba, tun ina jin kunyar na je na yi itace shi kuma ya fita siyar da ruwa har ya zame min jiki, sai na kwana biyu uku ban yi wanka ba, wasa wasa har nai sati kuma babu wanda ya kula ko ya damu da hakan, a hakan ma har na ke ganin na fi wasu tsafta, daga bodinga mahaifina ya rika shigowa cikin sokoto yana haduwa da wasu fulani da kuma buzaye, idan ya dawo sai ya rika ba ni labarin sokoto ita dai kamar kamba tana da tarin yan nijar da yawa a ciki, ya fada min cewar akwai da yawa a cikin fulani da buzaye da suke rabawa a irin gidajen da ba a gama gina ba su zauna, sai nai sha'awar mu yi haka saboda ina son na dawo sokoto da zama daga haka muka tattara muka dawo sokoto, a talatar mafara muka fara sauka, a nan muka fara fakewa a wani tsohon gidan da ba a kare ba, ya cigaba sana'ar siyarda ruwansa, ni kuma ina kulla gida ina siyarwa, kwata kwata na koma kamar ba yar saurata ba, kalar fatata ta canja wahala ta rufe ni ga kuma cikin Lukman da na samu a wannan lokacin, ya sani laulayi har na haife shi, mijina yana nuna min kauna sosai yana kula da ni iya gwargwado, bama cikin matsalar komai domin yana kokarin kawo wa mu ci, har kuka girma ya sakaki a makaranta sai dai yana rasuwa komai ya canja mana Ataa kin sani.... ” Kuka take kamar yadda nima na ke kukan, hakika na sani na san lokacin lokacin da mahaifina yai bankwana da duniya ba tare da ciwon komai ba a cikin gida muna fira da shi sai kawai muka ji yayi shiru ya risina daga zaunen da yake muka jijjiga shi shiru Nana ta kira sunanshi ta zuba masa ruwa amman shikenan mai kasacewa ta kasance, bayan mutuwarsa muka muka siyar da baronsa da duk wani abu na sa muka bar unguwarsa zuwa gidadawa a nan muka kafa bukkarmu kamar yadda muka ga Baba yayi, muka zauna a gurin har zuwa lokacin da masu gidan suka bukaci abunsu, muka sake tashi, da haka mukai ta yawo zama guri guri Nana kuma na fita tai mana bara ta kawo kudin mu siya abinci, har muka fara zuwa tare da ita da muka tara mai yawa sai ta saka ni a makarantar Yakubu mu'azu ni na fara zuwa lukman kuma ya hakura sai gaba, kudin tsintsiya da kudin pta suka hana ni komawa makarantar sai na cigaba da ya islamiyar ita ma ina haruffa na daina zuwa saboda baran ya shiga kaina na, kuma wani lokacin da yunwa na ke zuwa na dawo, karatun ma sai ya daina zama a kana ya zama bana gane komai, Nana kuma bata damu ba saboda bara kawai ta saka a gaba. Da haka har karatun ya gagareni na daina zuwa gaba daya, sai Lukman da ke zuwa shi ma jefe jefi. Mahaifina yana son mu daga ni har Lukman da kuma Nana, na sani a dan zaman da nai da shi na rayuwar da na samu tare da shi ya nuna mana kauna, a kullum burinsa ya zai inganta rayuwarmu da ta Nana, yana yawan fada min cewar dadi na nan zuwa ko ba shi da rai za mu jidadi ni da Nana da Lukman, shi ya tafi Lukman ma ya tafi ni da Nana kawai muka rage. Gaba daya jin nai kaina yayi nauyi kuma yana ciwo, saboda tunawa da baya da kuma jin labarin Nana, sai dai bana ganin hakan a matsayin laifin da mahaifinta zai iya cewa ba zai yafe ba, wata kila yana raye ko kuma ya mutu Allah nasani, sosai zuciyata ta cika da kaunar Aliyu domin shine mutumen da ya fara maida ni mutum ya sa na maye gurbin duk wani abu da na rasa kuma yarda ya so ni yadda na ke, ba dan kyau na ko wani abu nawa ba, tsabanin duk wanda zai kalle ni ya so dan kyauna, Momy kuma ta biyo a sahu na biyu a kaunar da ta nuna min na son danta ya aureni saboda ya inganta rayuwarta kuma Rahma ta daina min kallon banza, yana da wahala a zamanin nan ace wani wanda baka sani ba kamar Momy da Aliyu su soka tsakani da Allah. Sai a yanzu na ke gane wasu abubuwan da Nana take hango min. Hakika zabuwa da iyaye akwai ciwo da damuwa, ni kaina da Nana ta kamu da ciwon nan ina ta tsoro da zullumin rabuwa da ita, ni kenan da ke tare da albarkata ina ga ita da guduwa tai ta bar iyayen? Sai yanzu na gano dalilin cewar da take tana son ta san hannun da zan fada kamin ta bar duniya, tana kuma tsoron gaba saboda tana tunanin ba iyakar kaddararta kenan ba, lallai ko kadan ta ga na kuma abu ya zo da sauki da ya zama kodarta kawai aka cire kuma har ta samu tattafin Aliyu ya nema mata magani ta warke. A yanzu kam na yarda da zancenta cewar kaddarar Aliyu ce ta zo a hannunta kamar yadda tata kaddarar ta zo a hannun Babana.     Labarin Nana be kara min komai ba sai tausayi da jinka da kuma ganin darajar zabin iyaye ko da kuwa mai cutarwa ne, matukar ka bata musu rai dole ne sai wani abun ya same ka ko da ko kadan ne, kaunarta na ji ta karu a raina da kuma son zama kusa da ita, domin a yanzu ni kadai ce wacce take da, kuma ita kadai ce wacce na ke gani na ji sanyi a raina wato uwata.    Daga har ita cikin damuwa da tunani muka kwana, washe gari bayan mun yi sallah na zauna nai yi ma Babana addu'a sosai daman na saba masa a sujida sai dai wannan ta musammance, domin na san a yanzu babu abunda ya ke bukata a tare da ni kamar Addu'a ta. Misalin takwas da rabi na shiga part din Momy na share komai kamar yadda na sabawa kaina Amina da Husna kuma suka shirya abun karyawa suka ba ni nawa ni da Nana. Na koma na kai mata, ruwan shayin kawai ta sha ta kasa cin komai fuskarta gaba daya ta kumbura, kana gani ka san a daren jiya ta kwana tunani kuma ta sha kuka. “Nana Babanki zai yafe miki matukar yana raye, shekaru da yawa ya isa ya saka zuciyarsa laushi ya fahimce ki” “Ba zai yafe min ba, na aikata kuskure na gudu saboda biyan bukatar raina be kamata wuya ta saka na koma ba” “Ba saboda wuya za ki koma ba, saboda kin yi nadama kin gane kuskurenki za ki koma” “Wata kila ma baya raye, abun kunya ne ace na haihu har dayan ya koma ga Allah mahaifina be san yayana ba, yayana kuma ba su san yan'uwana ba, ba zan iya komawa garin nan ba har abada, na barwa iyayena da masarautar Agadez abun kunya” Ajiyar zuciya na sauke ina sauraren motar da naji an faka harabar gidan, hayaniyar Amina da Husna ne yasa na tashi na leka window sai na hango Momy ta fito daga motar ita kadai ba tare da Aliyu ba, wata kila ya tafi gidansa gurin matarsa ko kuma ba yau zai dawo ba. Fitowa nai na tareta tare da rika jar jakar hannunta na bi bayanta, ita kuma tana ta min murmushi har muka shiga cikin falon, a nan ta zauna Amina ta debo mata ruwa suna ta daukinta kamar wacce ta shekara bata gidan, ita tana marmarin gwanin sha'awa uwa mai dadi. “Momy ya Aliyu fa?” Husna ta tambaya. “Ba yau ba yace zai kwana biyu kamin ya dawo” Momy na bada amsar zuciyata ta raya min wata kila da matarsa ya tafi shiyasa ba zai dawo yanzu ba. Ballantana na san idan Mama Fulani ta ji cewar saboda ni komai ya faru ba zata barshi ya dawo ba, a take na ji raina ya bace. Da abincin mu na rana na dawo part din mu ina jin cewar yanzu ne ma lokacin da ya kamata na auri Aliyun ko dan Rahma da Mama Fulani sai na ga idan mutuwa za su yi, ace irin tsanar da suke nunawa talaka Aliyu ya aure ni sai ya kenan? Kuma ina tunanin ta wannan hanyar ce kawai zan yi ma Momy tukuicin abunda tai mana, ita kadai ce hanyar da zan saka mahaifiyata cikin farinciki a yanzu na taimake ta ita ma ta sake jindadin rayuwa. Da yamma ina cikin shirin zuwa makarantar islamiya, Momy ta aiko tana kirana Siyama ce ta shigo ta fada min gana sanye da nata uniform din na islamiya sai dai na ta dabam kamar yadda nawa yaks dabam kasacewar ba makarantarmu daya ba. Kamin na shiga part din Momy na hango mutumen jiya wato ustazu nan yau ma yana cikin shigarsa ta mutunci da kamala. Ina shiga Momy ta ce min. “Wani na waje yana sallama da ke, wai yana neman izinin mu kamin yai magana da ke, ki fadawa Nana sannan ki je” “Momy ban iya fira ba, ko naje ban san mi zan ce masa ba” Na bata amsa a takaice wanda har cikin zuciyarta haka ne, idan na je ban san abunda zan fada masa ba, fira da wani a yanzu ina jin kamar ba zata min dadi ba, idan kuma na ce zan yi da gara duk mutanen da za su bude ba ki na furta kalmar so a gareni tabbas ko zai furta ko ya nuna zai zama babu kamun kai a ciki. “To kije ku gaisa inyaso sai ki fada mishi an tsayar miki da miji ko kuma kina da wanda kike so” Da wannan shawarar da ta ba ni na tashi na fita zuwa gurin mutunen, mun gaisa da shi cikin mutunci ya gabatar min da sunansa aikinsa da kuma inda ya ganni wai lokacin da na taso islamiyar nan har ya tambaye ni gidanmu. Kai tsaye na bashi hakuri kuma na fada masa cewar akwai wanda za a tsiyar min a gida, ya nuna min rashin jindadinsa da kuma yi min fatan alheri sannan muka yi sallama. komawa nai bq na dauki littafaina na wuce islamiya zuciyata cike da tunanin ko zuwa yaushe Aliyu zai dawo? Mi ya tsayar da shi a abujar? Ni dai sam ban jindadin rashin dawowarsa ba, ba zan kuma kira abun da so ba, domin ba ni tabbacin ina son Aliyu ko akasin hakan, sai dai na san akwai sabo wanda ko fada kake da mutum dole ne wani lokacin sai ka yi marmarinsa balle kuma yanzu da na fara gane amfanin abubuwan da yai min. MOMY POV. Bayan tafiyar Ataa islamiya Momy ta tashi ta debi yan gurin da Mama Fulani ta sako mata a kwali wato snacks da cake ta nufi bq da su, da far'arta ta shiga bq din yana wayance wa kamar komai bw faru ba, ta karanci damuwa a fuskar Nana sai dai bata maida hankaki akan tatauna da Nana akan matsalar ba, a zatonta abunda Muhseen yai ne har yanzu yake damunta. “Mun yi tafiya shekaranjiya ban fada miki ba, tafiyar ta safe ce shiya saka” “Babbu komi Hajjiya ya hanya?” “Al-hamdulillah, ga wannan” Momy ta mika mata plates din hannunta, sannan ta dora da dalilin zuwanta bq din. “Daman Daddyn su ne yace a fada miki kuma a nemi shawararki aji ta bakinki, wai yana son indai za ki amince sati na mai zuwa a daurawa Ataa aure da wanda take so ko waye ne, mun hanke wannan shawarar ne saboda hankalin kowa ya kwanta ita kanta hankalinta ya kwanta kin ga ko zuwa sallamar nan ba dadi ne ba, amman idan har aka mata auren dole kowa ya kama gabansa, kuma yi mata auren ba shi yake nufin hana ta karatunta ba no zata cigaba da karatunta a gidan mijin ko kuma a nan idan zai yarda” “Sati daya?” Nana ta nanata. “Nima kaina naga kamar abun yayi wuri, sai dai saboda kwanciyar hankali kowa ake son ayi haka, ina son ki manta da duk abunda ya faru ki tambayi Ataa wanda take so idan a kusa ne sai neme shi idan kuma nesa ne sai a san ta yi tun wuri, idan kuma kina ganin watan yayi tsawo za ki iya fadar lokacin da kike son a saka, nan da wata daya biyu uku ko shekara ma ko fiye da haka” “A a hukuncin da kuka yanke ya yi, waya sani ko zan kai gobe ma balle nan da wata daya ko shekara, fatar ko wace uwa ai yarta ta samu gurin zaman da ya dace da ita, Na gode sosai Hajiya” “Karki jin kunya ko nauyin komai Wallahi duk wani abunda nai saboda Allah nai, dan haka karki taba kawo wani abu a ranki, ni da ke an zama yan'uwa kuma zan mata komai kamar yadda nai alkwari In-Sha-Allah, idan tarewar a nan kusa ne ko nesa duk daya ne a gurina” “Allah ya saka da alheri” Sosai Nana ta so tayi ma Momy maganar tashinta, sai kuma ta ji nauyi saboda girman Abunda Momy ta zo mata da shi, idan kuma tai mata maganar a yanzu wata kila ba zata fahimta ba, sai kawai ta zabi aje maganar a cikin har na wani lokaci. ALIYU POV. be Momy sun koma tare ba saboda yana jin zaman sokoto yana gundirarsa, abunda Rahma tai masa kadai ya isa ya saka shi jin baya son zama gidan da suka kasance suna rayuwa a ciki su biyu, ga kuma tunanin cewar Ataa ba zata zabe shi ba, so yana ganin kamar komawarsa sokoto karin bakinciki ne kawai a gurinsa bayan wanda na Mama Fulani take masa a nan. Domin Abbah ya fada mata matukar aka tambayi yarinya ta amsa musu da cewar tana sonsa za a daura masa aure da ita sati mai zuwa. “Wallahi Aliyu ka ma ce ka fasa idan ba haka na zan yi wa yarinyar nan raashin mutunci, sai na sa ta raina kanta sai ta gwammace a haifo ta duniya ba, ba zan taba karbarta a matsayin suruka ba, na kuma zan taba son ta ba, kar kuma ta ce zata kira da wani sunan ko ta tako inda na ke, kuma idan aka daura auren nan sai na taka har sokoto na ciwa uwarta mutunci na ga wanda ya tsaya musu a garin sokoto, wai har da hada baki da Abbah kun ce sati daya ko? Saboda ayi saurin yin abun ai kana jin kasan yarinyar ba yar kowa bace kuma ba neman auren suke sun ga dan arziki, wai Aliyu baka ma kunyar ace yarinyar nan ce matar ka?” Daga ita sai shi ne a dakinta take mishi wannan fada, sai ya shafa kansa ya ce. “Ni kaina ban tsammaci haka ba Mama, amman ya za'ayi” “Baka ma san abunda za'ayi ba kenan? Abunda za ayi kawai ka fasa auren yarinyar nan domin ko na aureta ba zan bari ku samu kwanciyar hankali ba, ga yan mata nan ai babban abunda za akayi ka bawa Rahma haushi a yanzu ka auro wanda ubanta ya fi uban Rahma arziki, amman ba yar bara a titi ba, bara fa Aliyu bara” “To zan yi tunani Momy” Shine kawai abunda ya fada mata ya tashi ya bar mata dakin saboda Maganganunta basa masa dadi, sam be son ya ji mai zagin Ataa a yanzu. MUHSEEN POV. tun bayan da yai maganar da Nana a waya ya zuba ido yana sauraren abunda zai faru, yasan indai tana da hankali da tunani ba zata bari yarta ta zaba tsakanin shi da Aliyu ba, da ace Aliyu ya samu shi ya rasa kara dai su rasa gaba daya, domin shi be ga ta inda zai rika kallon Ataa a matsayin matar Aliyu ba, a cikin Familyn a yanzu haka yana ganin kamar abu ne mai wahala ya ce zai samu wacce ta yi mishi ta kwanta masa a rai kamar Ataa, shi da ya dade yana burin auren mace da abokansa zasu susuce idan sun ganta kuma mai jini a jika kamar Ataa yanzu kuma ace Aliyu ne madadinsa, har ga Allah ya hakura da aurenta amman baya son Aliyu ya aureta kara dai ace bata cikin familynsu gaba daya. Tun daga ranar da ya bawa Momy hakuri be sake yarda sun yi ido biyu da Aliyu ba, kwata kwata baya shigowa gidan a lokacin da ya san Aliyu na cikin gidan, idan ya shigo yana part dinsa sai Aliyu ya fita sannan zai fito, dukan abunda kunnuwanta suke son ji wanda Ataa zata zaba, idan shi ne zai yi farinciki sai dai ya cire rai saboda ya san ba zata zabe shi ba kamar yadda yake ganin cewar ba zata taba zabar Aliyu ba. ATAA POV. wasa wasa akwa kwashe kwana biyu har uku Aliyu be dawo ba, ban kuma ji Momy na zancen dawowarsa ba, sai dai bana wasa da zuwa makaranta na da lokaci yayi rashin fara bokon kuma sai ya fara damuna wanda na san da Aliyu na nan da yanzu ya saka ni ko ya samu wanda zai saka ni, domin ina ganin sha'awar yadda Siyama ta ke shiryawa ta tafi makaranta da safe har jin na ke kamar na bita. Ranar Alhamis ranar da Momy ta cika kwana hudu da dawowa daga Abuja, Daddyn ya dawo da rana ya aiko Momy da kanta ta kira ni ni da Nana, tun daga lokacin da na ji kiran sai gana ya soma faduwa domin ina jin cewar zai tambayi idan na yanke shawara ne. A part dinsa muka taru gaba dayanmu har Momy da ni da Nana da kuma Daddyn kansa. Ni da Nana muka zauna kasa Momy kuma tana zaune a kujera daya da Daddy, babu yadda ba tai ba Nana ta tashi ta zauna saman kujera amman Nana ta ki. Bayan Daddy yayi gyaran murya ya soma magana da Nana kamin ni. “Hajiya tace ta tatauna da ke akan maganar auren Aisha, kuma kim fahimta ina fatar ba mu danne miki hakki ko tauye ki a wani abun ba” “Babu ko kadan” “Mashallah, Aisha kwana ki na kiraki tun Hajiya bata nan na fada miki kije ki yi shawara ki fadi min kuma ki fadi a gaban kowa cewa ga wanda kike so, saboda kar ya zamana mun tauye miki hakki ko saka ki abunda be kamata ba ko kuma ba ki tashi ba a yanzu, dan haka muna saurarenki karki ji nauyin baki ko kunyar fadar komai ni na baki dama, idan ma ba ki da wanda kike so a yanzu ko kuma kina ganin kamar abun ya yi kusa za a iya daga miki kafa har zuwa lokacin da kike so” Kasa cewa komai nai kaina yai mugun nauyi har ya sauko min ciki ido, gaba daya falon ji nai yana juyawa gabana ya shiga faduwa. “Aisha... Ke mike saurare” Ya maimaita jin na yi shiru har na wani lokaci, yawun bakina na hade ina da motsa yatsuna a cikin hijab. “Yana da wahala ta iya furtawa, ba al'adar mu bace furtawa ka tsaye ka ce ga wanda kake so” Momy ta fada, sai Daddy ya ce. “Muhseen kike so?” Na girgiza masa kai alamar a'a. “Akwai wani wanda kike so ne?” “Kamal kike so?” Momy ta tambaya sai na girgiza mata kai a nan din ma ina hade yawu. “Kina da wani wanda kike so ne?” Na kasa cewa komai ko matsin sai na kasa yi. “Aliyu kike so?” Daddy ya tambaya. A take wata irin kunya da ban taba sanin ina da ita ba, ta rufe kai kasa da kaina gabana sai faduwa yake idonuwana suka cika da kwalla. Tasowa nai na baro musu falon da sauri kafafuwa har hadewa suke kamar za su tarde ni na fadi. Da gudu na nufi Bq na fada saman katifa na fashe da kuka na rashin dalili. ALIYU POV. Yana zaune falon Momy Husna ta kira, sai ya ki ya daga kasacewar yana cin abinci ne, after few minutes Amina da kira shi nan ma be daga ba sai da ya gama cin abincin, yana kokarin bulbula zuwa ya sha Maryam ta zo da waya ta miko masa wai Amina tana son magana da shi. Ya dade yana kallon wayar sannan ya karba ya kara a kunnesa yana kai ruwan a bakinsa. “Ya Albishirinka....” Shiru yai ya kasa cewa goro jinin zuciyarsa na gudu da sauri ya rika shan ruwa har kana jin wucewarsu a makoshinsa. “Ataa ta ce kai take so kai kai kai” Mikewa yai tsaye da sauri sai sa ruwan da ke bakinsa suka tsarke shi a take ya fara tari a gurin. Ya sauke wayar ya kalla ya sake maida a kunnensa. “Say it again....” “Ataa tace kai ta ke so, kuma mamanta ta yarda a daura auren wannan week din” Bude baki yai kamar zai yi magana sai kuma ya kasa, ya mikawa Maryam wayar ya shafa kansa ha zauna da sauri yana da mamaki, before yai sujada a gurin yana ma Allah godiya, then ya mike tsaye ya dauki wayarsa ya nufi motarsa Nasir ya kira ya fara labarta masa abunda ya faru. Sai shafa kansa yake yana ganin kamar ba gaske ba, ko da ma tirsasata akai a gurinsa ba komai ba ne zai iya kula da ita. Ba shi da wanda zai taya shi murna a nan daga Mama Fulani har Muhseen and he don't want to celebrate it with Ammy saboda kar Mama Fulani ta ji haushi. “Nasir za a samu jirgi yanzu?” Ya tambaya with full farincikin a ransa da jikinsa da ruhinsa. “I don't think so amman bari na kira na ji” “Now pls” Kamin Nasir ya kira ya fada masa cewar babu jirgin yau sai dai gobe har ya matsu. Haka nan kawai farinciki ya saka shi shiga mota ya zaga garin Abuja da kewaye sai murmushi yake kana ganinsa kasan yana cikin farinciki da jindadi. A gangan ya ki dawowa gida gurin Mama Fulani ranar dan baya son ta bata masa farinciki a yau. Da dare ya kira Momy baki har kunne ta kara tabbarta masa da hakan. Kasa kwana yai a daren saboda farinciki yana ta ganin Ataa a fuskarsa, kamin gari ya waye duk ya matsu. Tun 7 ya isa airport bayan jirginsu sai 10 zai tashi, a gurin Nasir ya same shi ya taya shi murna haka yai ta kira har ten sannan jirginsu ya tashi. Na dade ina kukan har na shigo ta same ni a dakin, hankalinta ya tashi sosai ganin kukan nawa ba na wasa ba ne. “Lafiya Ataa?” Tashi nai zaune Ni kaina ba zan iya fadar dalililin kukanawa ba, sai dai na kasa daina hawaye ina jin wani bakon yanayi na rabata har yanzu na kasa daina jin nauyin a kaina da kuma zuciyata ban taba sanin cewar haka ake ji ba ko kuwa dai ni na ji haka Saboda ban saba ba abun ya zamo min bakon al'amari? “Ba kya son shi?” Na kasa cewa komai. “Karki cuci kanki Ataa idan ba ki son shi ki fada na san yadda ake idan aka gabatar maka da wanda baka so, karki cutar da kan ki” “Ni ma ban san dalilin kukan ba, amman har ga bana jin wani kwankwanton ko tatamar zabar Aliyu da yai” Har lokacin da na ke maganar hawaye be daina sauko min ba. Murmushi Nana tai ta kai hannunta ta share min hawayen fuskata. “Ina fatar mijinki ne na har abada, kuma ina fatar zabin Aliyu ya zame miki alheri a rayuwarki, rayuwar da na ke miki fatan samu ina fatar ita ce a yanzu take rabarki, kuma fatar wannan zabin da kika yi ba zai raba kan iyalan gidan nan ba” A cikin raina na amsa da amin sannan na kwantar da kaina jikinta. Na kara fashewa da kukan, sai da nai mai isata na samu natsuwar ruhi da zuciya sannan na tashi na shirya na wuce makarantar islamiya, yau a inda na zauna jiya na zauna kusa da wata budurwa mai far'a wacce na zauna da ita jiya, sosai na maida hankalina gurin karatu amman na kasa karanta komai sai tunanin abunda ya faru nake har aka kusa ta shi. “Yau ba za ki biya ba?” Na dago daga tunanin da nake na kalleta. “Zan biya” “Na ga an kusa tashi ne, ban ma san sunanki ba” “Sunana Aisha” “Okay ni kuma sunana Asma'u” “Kai ashe ke mamana ce” “Ina da sunan Mama kenan?” “Eh sunan Mamana ne” “Eyee daga yau Mama zaki rika ce min” Na yi murmushi tare da tashi na nufi gurin da malamin yake zaune ana biyawa, na biya harufan da na iya ya kara min wani na taso na dawo inda na ke ma zauna sai yarinyar ta ba ni yasin kanzo wai ko ina so, rai na biya dan haka na karba ina lasawa na ji yaji kamar zan hauka ce da sauri na mika mata ragowar ina fiddo halshena waje ,sai ta saka min dariya ita da wata yarinya da ke gefenta. “Aisha Aliyu ta so ana kiranki” Malamin nan da Aliyu ya danka ni hannunsa ranar ne ya shigo yana fadin hakan, ni kuma ban kula ba domin ban dauka da ni yake ba duk kuwa da kasancewar ni yake kallo kuma na san gurin saka sunan form din daya tambayi ni Aisha Umar na fada masa. “Aisha Aliyu” Ya maimaita yana kallona sai na nuna kaina. “Ni...?” “Eh ta so ana kiranki” Na tashi ina ta tandar baki saboda yajin na fito na biyo bayan malamin sai ya juyo ya ce min. “Dauko littafanki?” Ba musu na juya na je na dauko na biho bayansa, ina ta mamakin dalilin kirana Aisha Aliyu da yai. “Kije waje ana jiranki” Na nufi gate din cike da tunanin mai kiran nawa a wannan lokacin da ba a tashi a makaranta ba. Ina fitowa ya hango Aliyu jikin motarsa sanye da kakanan kaya yana kallon inda na ke tsaye da alama daman ni yake jiran na karaso, wani irin tattausan murmushi da ban taba sanin yana tare da shi ba ya rika aiko min yana min wani irin kallo mai wuyar fassara, yayi masifar kyau saboda Murmushin ya kawata fuskarsa har sai da ya saka gaba faduwa, kasa karasawa nai a na tsaya a gurin gate din ina kallonsa sai ya gyara tsayuwarsa ya rumgume hannayensa a kirji yana ta kallona kamar zai cinye ni, daga bisani ya dago daga jikin motar ya daso inda na ke, kamin ya karaso nai kasa da kaina kunyarsa ta rufe kamshin turarensa kuma ya zagaye ni siffar zatinsa ta hana ni sukuni. Hannu ya miko min na san be saba taba ni ba dan haka na mika masa littafan hannuna sai yai gaba ya bar a gurin, sai da ya isa gurun motar ya bude front ya juyo ya kalleni sannan na fara takawa da sauri gudun kar wani ya fito ya hango mu daga dalibai ko malaman makarantar. Ina isa na shiga na zauna sai ya rufe motar ya bude gidan baya ya saka littafan nawa ya zagayo mazaunin direba ya shiga yai mata keys muka hau babban titin unguwar, na yi zaton ko gida zai maida sai na ga mun wuce hanyar gida sai tafiya yake da ni, ni ko sai tandar baki na ke saboda yajin da na ke ji tun ina yi a hankali har sautin ya fara fitowa, da sauri ya maido da hankalinsa gurina kamar ba tukin mota yake ba ko kuma na ce ba a kan titi mike ba. “Kin ji ciwo ne?” Na kasa magana. “Ko yaji kika ci?” Na gyada masa kai alamar eh, sai ya faka motarsa gefen titi ya fita daga motar ya tsallaka titi ya shiga wani shagon be dade ba ya fito rike da leda ya dawo cikin motar, da kansa ya bude ledar ya fiddo gorar ruwan mai sanyi ya bude ta ya miko min. “Na goge” Na fada ina kokarin karbar ruwan, sai ya saka min murmushi as respond ya kai ruwan a bakina na sha ka dan na rike sauran. “Sun ishe ki?” Ya tambaya yana ta kallona kamar mai kula da yadda na ke shan ruwa, sai na gyada masa kai hannunsa ya kai ya karbi ruwan ya tashi motar da hannunaa daya dayan hannun kuma yana kurba ruwan. Yawo ya rika yi da ni a cikin garin sokoto wasu unguwannin na sansu wasu kuma ban sani ba, ni dai ban tambaye shi inda za muje ba nawa idone kawai. Sai da muka yi nisa sosai sannan ya faka motarsa gefen titi ya kwantar da kujerarsa ya juyo da fuskarsa gafena yana kallona, na yi zaton wani abun zai yi ko ya ce sai na ji shiru be ce min komai sai idonsa da ya tsare da su, mi kuma na kasa daga kaina na kallin gefen da yake ma balle kuma na iya hadu ido da shi. “Ki yi hakurina da kallona, yau ji na ke kamar na hade ki ji na ke kamar na bude miki zuciyata ki shige na rufe, ji na ke kamar a cikin jinina aka halittoki, komai ya zo min a babin da ban yi zato ba, ban san wace karmar zan fada da zata gamsar da ke irin kaunar ki da na ji a raina ba” Ji nai kaina yayi mugun girma, ban tana jin kunyar Aliyu kamar na yau ba, ban taba jin wani kalami mai girma daga bakinsa kamar wannan ba, bayan wacan furucin da yai min yau ma ya kara min wani wanda ke dora wacan a babin da zai tabbatar da wacan zancen na farko, a wacan karon na yi zaton yana rokona ne saboda kare Momy da son cika mata burinta, sai dai kalaman da yai min a yanzu da irin shaukin da yake ya sauya tunani na. “Kar a tashi makaranta.....” Na fada numfashi na fita daker kamar wacce aka taushewa zuciya. “Na fadawa Malamin ku gida zan kai ki fita za ku yi da Momy” “Amman yanzu an kusa tashi ai....” Na furta still numfashin nawa na gargada, sai ya sake dauko ruwan da ke tsakanin ni da shi ya bude robar ruwan ya miko min. “Sha” Na karba da sauri na kai robar ruwan a bakina ina ta sha kamar ba zan daina ba har sai da na soma tsarkewa sai yai saurin rike robar ya ciro tissue ya mikon. “Sannu” Na karba na goge ruwan da suka zuba jikin hijab dina sannan ta zuke gulashin motar na wurgar da shi waje, gaba daya na tsawwala ina ta jin motar ta mana kada kuma kunyarsa ta rufe duk na bi na rude. Shi kanshi ya lura da hakan, sai ya gyara kujerar ya soma toka motar muka hau titi. Kadan kadan yake tukin har muka isa gida, a bakin gate din ya faka motarsa, ya bude motar ya fita ya zagoyo gefena ya bude min motar “Babyna fito ki shiga gida” Na san ma'anar Baby yana nufin jaririya mace, wato yana nufin ni jaririyarsa ce kenan. Na fito daga motar kaina a kasa sai da ya rufe motar sannan ya bude gidan baya ya dauko min tittafaina ya mika min sai da na mika hannuna an karba sai yaki saki “Thank you so much Love, kin cece ni na zan tana manta wannan alfarmar ba, kin cancanci komai daga gareni I love you so much” Har zan sakar masa littafan sai yai saurin sakar min ya tsaya yana kallona har na shige cikin gidan. Ban taba dawowa a irin wannan lokacin ba ana ciran sallah magariba, idan ma Nana ta tambaye ni ban san mi zan ce mata ba. Ina shiga bq din sai na samu Nana bata nan sai dai dakin a bude yake cikina na shiga na cire uniform dina ya shiga bandaki nai alwala, ina cikin Sallah Nana ga shigo dakin ita ma ta wuce bandakin tai alwala ko da ta fito na sallame ina tasbihi da hannuna. “Tun dazun kika dawo ko? Daman Hajiya ta ce kila ma kin dawo kika zauna a dakin ke kadai kina jin kunyar shigowa bangarenta” Na yi murmushi cike da jindadi domin na san idan ta san na kai magariba dole ta tambaya abunda ya tsayar da ni kuma ban san abunda zan ce mata ba. “Hajiya ce ta aiko aka kiranin na je can muka yi hira wai na daina zama ni kadai a nan” “Allah sarki Momy ai tana da kirki” “Tana da kirki sosai kam, kin yi dacen suruka indai abun ya bi haka” Wata kunyar ce ta rufe ni ban taba tsammanin idan na yi wa mutun irin wannan maganar kunya tana rufe ba duk kuwa da kasancewar uwata ce amman na ji kunyarta sosai. ALIYU POV. ido ya kura mata yana ta kallon tafiyarta har ta shige ciki, wani irin abun yake ji marar misaltuwa lallai ya yarda kuma ya tabbatar a yanzu kam yana son Ataa so ba na wasa ba. Motarsa ya shiga ya dauki hanyar gidansa, sai da ya shiga ya faka motarsa sannan ya fito ya doshi masallacin unguwar yai gabatar da sallah magariba da ya fito sai ya tsaya bakin masallacin sai da liman ya fito sannan ya yai saurin taronsa ya mika masa hannu suka gaisa. “Ah Alh Aliyu ya gida ya aiki” Haka yake kiransa Alhaji Aliyu ba dan komai sai dan tarin dukiyar dake saka kowa ganin kimarsa da jin kunyar kiran sunansa kai tsaye. “Al-hamdulillah” Aliyu ya amsa sannan ya saka hannunsa aljihu ya ciro duka kudin aljihu da na Wallet dinsa ya mikawa liman din. “Dan Allah amin sadaka da wannan a bawa mabukata” Da hannu biyu liman ya karba yana bude baki cikin tsananin mamaki domin ba kasafai Aliyi ma ya cika tsayawa ya gaisa da mutane ba balle kuma har ya mika wani abun da sunan taimako. “Masha-Allah Mashallah, Allah ya saka da alheri Alhaji Aliyu Allah ya biya bukata ya kara bude ya sakawa rayuwa albarka, Wallahi ka taimaka a wannan hali da mutane suke ciki ai taimakon ake bukata ta ko'ina” Har cikin ransa ya jidadin addu'ar liman after Momy dake masa addu'a kullum sai kuma Nana da ta taba masa a asibiti yau ma an sake masa, duka biyu kuma sanadin taimako ne ta uwa kuma ta kauna ce, sai ya ji natsuwa da kwanciyar hankali sun rabi ruhinsa. Cikin gidansa ya koma ya bude freezer ya dauko ruwa ya sha kadan ya aje sauran ya dawo saman cushion ya kwanta kamar wani sabon ango haka yake jin kansa gaba daya ya manta da komai da ke tare da shi Ataa kawai yake gani da kuma irin rayuwar da zai yi da ita, lokaci zuwa lokaci yake murmushi yana shafa kansa da fuskarsa, har mamakin yadda farinciki ya cika masa zuciya yake. He don't think zai iya biyewa Momy ko wani ma cewar after aurensu za tai karatu shi ji yake kamar kar kowa ma ya kara ganinta daga yanzu, he i can't wait ya ga ta zama halalinsa ta yadda zai rumgumeta a kirjinsa ya sumbace ta. Tashi yai zaune ya nufi dakinsa ya doro wata alwalar ya fito ya nufi masallacin dazun yai sallah, mutane sai kallonsa ake ko zai sake rabawa wasu kuma dan ya san da su, har da masu ba shi hannu ya gaisa da su, a da he can't shake his hand with anyone indai talaka ne amman a yanzu sai mika musu hannunsa yake suna gaisawa kamar ya manta waye shi. Yana shigowa gida ya sake shiga dakinsa ya dauko wasu kudin ya saka aljihunsa sannan ya fito ya shiga motarsa horn daya aka bude masa gate sai ya tsaya daidai gurin mai gadin ya ciro kudin da za su kai eight to nine thousand ya mika masa, a take mai gadin ya washe baki ya fara zuba masa addu'a shi kan be shi ta kansa ba ya dauki hanyar gidansu Momy. Har ya faka motarsa bq din su Ataa yake kallo ji yake kamar ta leko ya ganta, ya dauki lokaci a haka sannan ya bude motar ya fita ya shiga part din Momy sai wagen bq din yake kmar ance masa fitowa za tai. Hannu ya kai ya tura kofar falon ya shiga fuskarsa da murmushi kamar ba shi ba, duka suna zaune falon suna ci abinci a plate daya da Momy, Amina Siyama da kuma Husna. Tuwon shimkafa ne miyar kuka da man shanu sai kamshi yake. Suna kallonsa ya sakar musu murmushin farinciki, Momy ta ce. “Ai na dauka ka bata a jirgin ne, tun safe ba a samun wayarka kuma ba ka shigo ba” Sai yanzu ya tuna wayarsa a flight mode take. Zauna yai a kujera yana dariya. “Momy kin san me Wallahi na manta sam wayata a flight mode take kuma ban cire ba, kuma da wani dan abun ne ya rike ni bayan na sauka a nan” Da dai daya kannensa suka rika mika masa gaisuwa yana amsa musu, sannan ya saka hannunsa aljihu ya ciro kudi ma su yawa ya mikawa Amina. “Gashi nan ku raba” Ya sake saka hannunsa ya ciro wasu kudin ya mikawa Siyama. “Idan kin gama cin abinci ki kawai mai gadi” “Wow Ya Aliyu na cikin farinciki ni na maka albishir fa” “Thank you Husna i love you” Ya fada yana murmushi. “I love you too Yayana” Sannan ya kalli Momy ya ce. “Thank You Momy” “For what?” “For everything” Murmushi tai ta cigaba da cin tuwonta. “A zubo maka?” “No Wallahi bana iya cin komai tun jiya da aka fada min har yau bana jin yunwa” “Taf to Yayana idan aka daura maka aure fa” Husna ta fada. Dariya yai ya kwantar da kansa jikin kujerar domin ba zai iya fadar abunda yake ji a yanzu ba ma balle kuma idan ta zama halilinsa. “Momy wannan Assabar din ne ko?” Momy ta kalli Siyama tana bata amsa. “Eh In-Sha-Allah” “Amman ba yi ai iv ba ko sai gobe gobe fa Friday?” “Ni ko mutun biyar suka daura min aure ya wadatar ni dai a daura din kawai dai shine matsalata” Ya fada kai tsaye a gaban Momy. Yadda take ganin Aliyu yana nuna son Ataa daga lokacin da tai masa maganarta zuwa yau kamar wanda be taba aure ba aka hada shi da wace yake so kuma a dauke masa yin komai haka yake. Misalin takwas Daddy ya dawo, bayan ya shiga part dinsa ya huta Momy ta kai masa abinci y ci sai Aliyu ga shiga gaishe shi, nan ma fuskarsa da Murmushi tana nuna farincikin da yake ciki. “To sai ka rike yar mutane da amana kuma kai adalci dan kasan ba ita kadai ce ba, kar son wata ya saka ka danne hakkin wata ko nunawa ta kiyayya, ka ji tsoro Allah” “Na gode sosai Daddy In-Sha-Allah Allah zaka same mi mai adalci da rike amana” “Allah ya hada kanki ya kawarda fitini kuma ya ba ku zama lafiya” “Amin” Ya amsa sannan ya taso ya dawo part din Momy, sai kusan sha biyu dare ya bar gidan a harabar gidan ya tsaya ya dade yana kallon bq sannan na koma gida, da farinciki ya kwana ya tashi ya kuma dawo gidan Momy, duk yadda ya so ya saka Ataa a ido yau be saka ta kasacewar islmiya kuma ta labe a bq abunta ta ki fitowa. Haka ya sake wuni a gidan domin ba shi da inda ya fi nan, ga zuciyarsa kuma ta kwadaitu da son ganin Ataa kamar wanda be taba ganinta ba. After sallah isha'i Daddy ya dawo, ko hutawa be yi ba ya kira Aliyu a waya ya fada masa yana son ganinsa, a natse suka gaisa da Abbah before ya dora da. “A masallacin juma'a na Muhammadu Maccido da ke amir yahaya za a daura auren, dazun muke magana da Alhaji Sulaiman na fada masa tun da ba gayyato mutane za'ayi sosai ba kara a daura auren a friday kawai a huta” “Daddy gobe Friday fa?” A rikice Aliyu ya fada yana kallon Daddy da wani irin farinciki marar misaltuwa. “Yes” “Daddy thank you so much Allah ya saka musu da alheri” “Amin” Daddyn ya amsa yana bude jaridar hannunsa. Daga haka ya taso ya dawo part din Momy, sai murna ta kaure a falon shi da kanensa da Momy domin suna son farincin dan'uwansu duk kuwa da irin hade musu fuska da yake sai dai sun san yana son su kuma yana musu duk abunda zai saka su farinciki. Be bar gidan ba sai kusan goma na dare, har ya isa gida zuciyarsa bata daina zumudi da son ganin Ataa ba, ji yake kamar ya hanyo goben ya matso da ita ta zama yau ma a daura musu auren tun a yau ba sai gobe ba. Sai da ya huta ya sha Lipton sannan ya kira Nasir na sanar da shi komai kuma ya fadawa Nasir da sanar da wasu friends dinsa, shi kuma ya turawa wasu da kansa a take aka fara kiran wayarsa kowa ya ji abun daga sama. A cikin daren Aliyu ya sake buga wayar Nasir ya fada masa ya idan zai zo dauren auren ya zo masa da expensive ready-made da shoes da cap, yana da sabbin tufafi a nan wadanda be tana sakawa ba, amman ya fi son yai siyo wasu saboda dalili zai jindadi da natsuwa. MUHSEEN POV. Ji yai kamar ya rumtse ido ya bude ya ga komai na duniyar nan ya tarwatse cikin kuwa har da auren da Aliyu da Ataa da jin labarin na hana shi sukuni da walwala, wani irin bugawa zuciyarsa take da ace akwai abunda zai yi ya hama faruwar auren a yanzu da yayi, domin sai a yanzu yake jin cewar yayi ganganci kuma yayi sake na saurin sakarwa Aliyu ragama. He can't believe ya rasa Ataa kenan har a bada, taya zai rika kallonta a matsayin matar Aliyu a cikin familynsu? “Be ma kamata tun farko nai hakan ba, shikenan shi ya samu kyakkyawa kuma wacce na ke so, ya ji dadin kara fadin rai” Ya fada yana wulgar da kofin tangaran din dake hannunsa a take kofin ya fashe. Wani irin fushi da bakinciki yake ji marar misaltuwa kamar ya haukace yake jin kansa gaba daya ya kasa natsuwa ya saka sukuni. Ta bangare Mama Fulani ma fada kawai take ta inda take shiga ba ta nan take fita ba har da cewa zata shirya taje sokoto sai da Abbah ya taka mata burki, gaba daya ta hana kowa zama lafiya ciki kuwa yar da yayanta haushin auren da zaba daura gobe ya addabi zuciyarta. Ammy ce kawai da yayanta suke murnar abun domin ta san cewar Ataa ta samu mijin daya dace da ita kuma wanda zai kula da ita, abun har mamaki yake ba su yadda Aliyu ya fada son Ataa a haka, a daren ita da yayanta kwana sukai suna ta zancen masu cewa daman sun lura da kaza da kaza suna ta yi. ATAA POV. Na kwana da tunanin Aliyu mamakin kalamansa har suka saka ni murmushi ni kadai, washe garin ranar da gagan na ki fita ko'ina saboda kar Aliyu ya gan ni ko kuma ni na ganshi abinci mu da komai Momy aiko mana tai kamar yadda ta saba ko da yake wani lokacin ta kan aiko tace na zo na dauka. Ban wani ci abinci sosai ba na kwanta, sai Momy ta aiko tana kiran Nana, ni dai ban san lokacin da ta dawo ba domin bachi yayi gaba da ni, washe gari bayan na yi sallah asuba na zauna sai da rana ta fito sannan na nufi nufi part din Momy, wani abun mamaki sai na samu kaina da kasa shiga ciki, sai kawai na juyo na dawo kamin na karasa motar Aliyu ta shigo harabar gidan yana sauri ya fito daga motar yai min magana ni kuma yai sauri har da hadawa da gudu na shige cikin bq din. Ban fadawa Nana komai ba sai dai tana ganina ta san ban shiga part din ba domin ban isa ace na shiga har na yi sharar na fito ba. Amina ce ta kawo mana abun karyawa a maimakon Siyama wacce ta saba kowa mana, sai da ta gaisa da Nana sannan ta fada min cewar idan na gama karyarwa na shirya zamu je gidan wata Hajiya Ramatu kawar Momy wai a can za mu yuni. Ina ta mamakin fita da safe haka kuma wai mu wuni a can amman kuma ta taimaka min ko ba komai bana son haduwa da Aliyu a yanzu gashi yau friday kamar jiya ba zuwa makaranta ake ba. Misalin goma da yan mintuna mu kabar gidan a lokacin har na fara ganin bakin fuska a gidan cikin kuwa har da abokinsa Nasir. A gidan Hajiya Ramatu muka wuni ni da Amina wanda ban san dalilin hakan ba, kuma na kasa natsuwa saboda jefi jefi sai Hajiyar ta kira ni Amarya sai murna take da alama itama tana son auren kamar yadda aminiyarta Momy take so. Bayan gama sallah azahar ina zaune ina kallon arewa24 suna kokarin karkare wani shirin hausa mata da miji Amina da shigo da waina a a plate da miya ta aje min “Gashi nan ki ci wainar daurin aurenki yau an daura miki aure Ataa igiya uku ta hau kan ki, Kin zama Mrs Aliyu Aliyu......” Kamar wacce ta fara ji a yau haka na ji maganar wani kallo na ke mata da ke nuna cewar sam ban fahimci inda zancen ta ya dosa ba, sai ta kama kumatuna ra ja. “Seriously yau friday aka daura aurenk after Jumma'at prayer congratulations you're now our sister-in-law” Ta fada ta rumgume ni cike da murna. Ni dai daga turanci da bana ji har hausar ban iya gane komai ba domin a rikece na ke. Sorry two days ina post a night 😑🙏 *Z A K I -it's not free, pay 300 to 0314795884 Abubakar Gt bank, then send the evidence via 08036126660* Ba kowa da kowa aka gayyato a gurin daurin auren ba, sai makusantan Aliyu ciki kuwa har da abokansa duk kuwa da wasu ba su samu zuwa ba bikin ba kawai sun samu sakon ne daga Aliyu wasu kuma daga Nasir gashi lokaci ya kure ba su samu zuwa ba. Sun samu addu'a sosai albarka jama'a kasancewar massallacin juma'a kuma babban masallaci wanda mutake ke taruwa sosai bayan daura auren nasa aka daura na wasu mutanen biyu.   A cikin mutanen da suka samu halartar daurin auren har da Kamal wanda Nasir ya sanar da shi amadadin Aliyu, baya farinciki da auren Aliyu da Ataa sai dai kuma baya bakinciki, domin ya san daman Aliyu yana son ta kuma tunda aka ce tana gidansu daman yasan tsakanin Muhseen da Aliyu dole sai ta auri daya. He know what he did to Mama Fulani be kyauta ba, Mahaifiyarsa ma ta masa fada akan hakan kasancewar Mama Fulani kawarta ce kuma makociyarsu bugu da kari kuma mahaifiyar Aliyu domin kamar uwa take a gurinsa. Daman yana neman hanyar da zai shirya da abokinsa kuma ya bashi hakuri kan abunda ya faru, sai dai ba zai iya iya kiran Aliyu kai tsaye ba sanin halinsa na wulakanci zai iya neman ya wulakanta shi ganin ya kawo kansa da kansa kamar yadda yake ganin Mama Fulani ma zata iya masa.   But sanar da shi da Nasir yai cewar Aliyu yana gayyatarsa dauren aurensa ya sa bari duk wani aiki da yake da shi a ranar friday din ya halarci daurin auren, yana ga jin kamar ace shi ne ya auri Ataa. After daurin auren aka wuce shukura hotel aka ci abinci mai kyau drinks ma sai wanda ran mutum ke so. Ango ya sha kyau shaddar jikinaa ai wani haske take yana wani maiko kana gani ka san shaddar masu naira ce, ko masu nairan ba kananan ba, farar shadda ce wacce ta sha aiki, ga wasu expensive shoes da be taba zuba zuba kudi mai yawa ya siye takalmin da suka kai wadanda Nasir ya zo nasa da su daga Abuja tsada ba, hular kansa kadai tana siyen tufafin wani mai kudin kala goma. Zuciyar Aliyu kal ransa fes kamar babu abunda ya taba bata masa rai a duniya, wasu family friends dinsa har mamakin yadda ya sake da mutane yake ta dariya suke domin sun san ba halin Aliyu ba ne. Amman sai dariya yake baki har kunnuwa yadda yai muran da zuwan Kamal sai ka dauka ma wani abu be shiga tsakaninsu ba, farinciki aure ya saka ya manta da komai.   After lunch a hotel wasu suka kama hanyar Abuja wandan suka zo daga can ciki kuwa har da Abbah da wasu aminansa, yan wasu garuruwan ma suka kama hanya, har da yan Yola wato yan uwan Mama Fulani domin sun san Aliyu dan Mama Fulani ne sai dai Abbah ne ya sanar da su ba Mama Fulani ba, har da kanen Ammy biyu da goma suke Kaduna sai da suka zo.    Momy tana gida tana fama da nata Familyn da kuma Familyn Daddy ana ta wasa da dariya sai tsarguwar juna suke ita da tabasanta da kuma tabansan Daddy, abun gwanin burgewa, Husna da Siyama da wasu cousins dinsu mata su suke rabawa baki abincin, a gidan an yi jalof din shimkafa da kuskus, fried rice, waina da kuma tuwan shimkafa. And su snacks cake da donuts. Drinks ko tun daga na zobo kunun aya, kunun waken suya, ginger da na waje babu kalar da babu, daga Candy Restaurant Momy tai order komai, sai ka dauka ma wunin biki ake ba wai daurin aure ne kawai ba. Yadda aka taru abun har Mamaki ya bawa Momy domin wasu dai bata san ta fada musu ba, musamman ma matan da suka zo na zaton ko har da wunin bikin ne. Komai na Nana Momy ware mata tai ta aika mata a bangarenta.    Sai kusan magariba Momy ta samu kanta, daman wasu daga familynsa da suka so yan matan sun ce a nan za su kwana, Husna da Siyama sai labari ake yana jindadi an hadu da yan'uwa, Amina ce kawai bata nan kowa sai tambayarta yake sai a fada musu tana can tare da Amarya, sai dai ba a fada musu inda Amarya take saboda Momy ta fadawa su Husna da Siyama cewar bata son a damu Ataa domin bata san da daurin auren yau ba kuma bata saba ba, ba karamin aikinta ne ba ta sakawa mutane kuka. ALIYU POV. Da kansa ya raka wasu friends dinsa airport yana ta musu godiya cikinsu kuwa har da Kamal, sai dai ya kasa sakewa yana ta jin kunyar Aliyu har sai da ya ga Aliyun ha wayance kamar ba shi ba, ko kuma ya manta da abunda ya faru sannan shi ma ya saki jikinsa har yai ma Aliyun sallama su kai shaking hands.   A  hanyar su ta dawo gida tare da Nasir yake driving yana sokonar Aliyu. “An daura auren nan dai hankali ya kwanta” “Wallahi kuwa yanzu hankalina a kwance yake fes ba ni da wata matsala malam” “Ango ango angon da ba Amarya” “Inji uban wa?” Nasir ya kyalkyale da wata mahaukaciyar dariya wacce ta saka Aliyu da kansa shi ma ya dara. “Ai kasan dai Momy ba zata baka amarya nan yanzu ba ko? Sai ta girma” “Girma? Ta girma a gidana na yarda dai ba zata tare a yau ba” “Kuma daidai ne ace yadda ka sha shaddar nan ajima a kai maka amaryar ka” “Na rantse da Allah kau, Nasir kai mugu ne Wallahi” Nasir din ya sake saka masa dariya har da buga sitarin motar. Aliyu yai murmushi yana cire hularsa ya shafa kansa, sai a yanzu yake jin cewar lallai yayi dacen auren Ataa daman yana son yan latsu wato karamar yarinya kamarta wance bata iya komai bata san komai ba bata waye ba a komai ba, kuma bata taba soyayya ba, he know littafinsa ne zai bude a kwakwaltar da kuma zuciyata domin ya san duk abunda ya koya mata shi zata haddace ya zauna a kanta.    A harabar gidansu Momy Nasir ya faka motarsa ya riga Aliyu fita ya shiga ciki domin gaisawa da Momy daman tun da ya diro garin be leko nan ba, kai tsaye na nufi gurin abokinsa, daga can suka nufi gurin daurin aure kamin su soma hidimar abokansu.   Aliyu na kokarin fita motar wayarsa tai vibration alamar kira, ciro wayar yai daga aljihunsa sai ya ga bakuwar number yar waje saman screen din wayar na nuna masa ana masa kiran ne daga Dubai. Kai tsaye ya fahimci cewar mai kiran tasa ba kowa ba ce face Rahma. Murmushi yai ya danna picking ya kafa wayar a kunne. “Hello Dear ya Dubai? Hope hutun yayi miki dadi?” “Aliyu ka yi aure?” Ta tambaya a sanyaye gabanta sai faduwa yake tana son ya amsa mata da capital NO. “Yes Yau din nan aka kara dora min wani nauyi da kuma hakki, daraja ta ta dagu daga mai mata daya zuwa biyu” “Aliyu?” “Ana wasa da aure ne Rahma? Ai kin san ko zan miki wasa da komai ban da aure ko?” “Aliyu ina nufin aure na sunna a daura maka irin wanda aka mana” “Irin shi akai mana da kanwarki Aisha a yau” “Aure fa Aliyu? Wallahi ka ci amanata ka cuce ni Aliyu ba zan taba  yafe maka ba, tun ina da rai zaka fara nuna min hakinka ba ma sai na mutu ba?” “Wacce zata iya zaman aure ta kula da mijinki kawai na aura” Ta tsinke wayar ba tare da ta sake cewa komai ba shi kuma ya maida wayar aljihu ya nufi cikin gida. Yana shiga wasa da dariya zoyata tsakaninsa da tabansansa ya tashi sai dai duk yadda suka tsarge shi sai dai yai dan murmushi baya cewa komai, daman can haka yake indai ya hadu da abokan wasa sai dai yai murmushi ko yar dariya kadan idan akai wani abun.   After sallah magariba Nasir ya shiga gari domin ganawa da wasu friends dinsa. Aliyu kuma yana gida gurin Momy sai tunanin inda aka kai Ataa yake, domin ita kadai ce abunda idonsa ke son gani a yanzu, muradin zuciyarsa. Amman baya jin zai iya tambayar kowa ina Ataa ai da kunya. Sai dai ya duba yaga duka sisters dinsa suna nan ban da Amina dan haka ya tambaya. “Ina Amina?” “Wai tana can tare da Amarya yau duk abunda akai ba da ita akai ba” Wata cousin sister dinsa ta fada, a take ya mike tsaye ya fito harabar gidan ya kira Amina. “Hello Ya Aliyu” “Kina ina?” “Ina ina ina kebbi” “Wasa na ke da ke?” “Ya ina sama road” “Ni da Ataa” “Aisha... Anty Aisha” Ta kara da Anty gaba daya. Ya san mutane biyu ne a sama road Mama Zuwaira wato kanwar Momy sai kuma Aminiyarta Hajiya Ramatu. “Gidan wa?” “Idan Mama Ramatu, amman Momy ta ce karna fadawa kowa inda muke har da kai” Ya katse wayar ya ya koma cikin falon dan karbo keys din motar Momy domin ya baro tashi motar da duka keys dinsa a main house. A falo ya tsaya ya aika Siyama ta karbo masa key motar Momy, sai Samira ta mika masa nata. “Ga tawa idan fita za kai” “No” Sai da Siyama ta karbo masa na Momy sannan ya fice daga falon ya nufi motarta ya shiga sai da ya cire babbar rigarsa ya jefa seat din baya sannan yai ma motar key ana bude masa gate ya dauki hanyar sama road yana ta tsara yadda zai ce idan ma yaje, daga karshe yai yanke shawarar tsayawa a waje ya kira Amina ya ce ta masa dabarar fitowa da Ataa. ATAA POV. Na kasa yarda cewar an daura min aure a yau ai ba yau bane gobe ne Saturday. “Ko dai ba ni ba Amina ba sai gobe ba” “Yau akai Daddy ya canja sharawa ne kawai dai ba a fada miki ba ne, amman an fadawa Mama cewa da Nana jiya da dare” Rungume hannayena nai ina jin komai kamar ba gaske ba, murna zan yi ko kuka sai na rasa na farawa, Amina kan sai murna take har da nuna min hotunan daurin aure da akai yana tare da friends dinsa. Ni dai har bana iya gani da kyau na zama kamar wata dabam ba ni ba, duk wani abu da akai a can gidan sai da Momy ta dibo ta aiko mana, ni dai ko wanar ban iya ci ba yunwar rana ma sai ma nemeta na rasa, sai yanzu na gano dalilin sa a kawo ni nan da Momy tai. Lokaci zuwa lokaci Amina take mita wai ita kadai ce a nan sauran duk suna can suna da hidima. Da yamma Hajiya Ramatu ya hada min ruwan wanka mai kamshin gaske ta sa aka kirana na shiga bandakinta nai wanka ina fitowa ta ba ni wani bakin lace na saka ta fesa min turare sannan ta zaunar da ni a dakinta ta zubo min tuwo ta kawo min wai na ci. “Na koshi” “Daure dai ki ci ji idonki duk ya fada tun karin safe fa” A dole na saka hannuna na soma ci ba dan ina jindadin tuwon ba domin ni ko sinadin miyar ba na ji, aure kawai na ke ta tunani wai an daura min aure, ji na ke kamar na saka kuka kuma babu damar shi gaba daya na ji na damu kuma ba damuwa ba, na saka sakewa a gidan kuma bana jin zan sake a ko'ina ma.   Bayan sallah magariba ina zaune dakin ni kadai sai ga Amina ta shigo ta matso kusa da ni tana min magana kadan kadan. “Ta so ki rakani wani guri kamin Mama Ramatu ta dawo” Da sauri na tashi daman zaman dakin ya isheni ina nema inda zan sha iska na ga wasu abubuwan ko zan sake. Hijab ta dauko ta bani na saka daman ita akwai veil a jikinta sai kawai ta rika hannuna muka fita sai leke leke take kar Hajiya Ramatu ko yayanta ko wasu yan gidan su gamu, muna kawowa babban falon Wata yarinyar Hajiyar ta ta ganmu. “Ke ina za ki je da ita?” Amina tai mata alama da tai shiru kai Hajiya Ramatu ta ji. Ta ja hannuna muka fice daga falon muka bar yarinyar tana dariyar da ban san dalilinta ba. Gaba daya muka fice daga gate din sai da muka yi dan nisa muka kawo gurin wata mota sannan ta tsaya jikin motar ta bude min front seat. “Shiga” Kin shiga nai hango Aliyu a ciki rike da wayar da ke haska fuskarsa yana kallona. Amina bata tsaya bin ta kaina ba ta juya da sauri ta nufi hanyar gida, bude motar Aliyu yai ya fito ya zagayo inda na ke, na yi zaton ko motar zai saka ni sai nai saurin rufe gambun motar na juyo na fara takawa sai ya sha gabana yana murmushi. Takowa yake ta yi ina jin baya yana matsowa har na isa jikin motar gabana sai faduwa yake ban taba jin kunyarsa da tsoron a raina kamar na yau ba, domin duk wani tsoro da nake masa na gudun duka ne ko ba cin rai a yanzu kuma ban san na minene ba. Matseni yai sosai har ina iya jiyo numfashinsa kamar yadda yake jin nawa sai nai saurin rufe idona gam, hannayensa ya saka ya kama hannuna ya saka yatsunsa cikin nawa, dayan hannun ma haka yai masa sannan ya jinginar da fuskasa jikin tawa fuskar, hancina da na shi suma goga juna, goshinsa da nawa a hade ya lips dinsa kuma a saman nawa, numfashin da nake fitarwa yake shaka idan ni kuma zan shaka sai ya fido da nasa na shaka a haka muka dauki tsawon lokaci muna musanyar numfashi, jikina sai rawa yake sosai domin ba a taba min haka ba, sanyi na ji a kumatuna, idanuwana na bude sai gashin idona ya taba nasa, na yi zaton shi ne yake hawayen ashe ni ce, a hankali na ji lips dinsa a kasan idona yana sumbatar inda hawayen nawa suke taruwa. “Ali...Al.... ” Na kasa kiran sunansa balle na ce ya daina, sulale nai kamar zan duka kasa sai sai yai min masauki a kirjinsa ya rumgume ni tsantsan ko motsin bana iya yi, kaina ma saitin zuciyarsa ina jin yadda take bugawa da sauri. Sai da aka  fara kiran sallah isha'i sannan ya sake ni ya leki fuskata sai kuma ya kama hannuna ya dora a kirjinsa. Ya saka dayan yana murza yatsuna a hankali sai kallon fuskata yake. Ni kuwa numfashina sai gargada yake kamar zai fita daga jikina shigarsa ma daker ne, saurin lumashe ido nai na yi sai na ji sanyin yawunsa a lips dina, halshensa ya saka a cikin bakina, ba tsosar lips dina yake ba ba kuma tsutsa zai yi ba, a tsakanin lip din kasa da na sama ya zira halshen yana goga min dogon hancinsa a hancina. A take na fashe fa kuka saurin dagawa yai da kansa ya matsa baya sai ta juyar da ni ya jinginar jikin motar ya kwanto bayana ya rumgume ni. “Wallahi ina cikin farinciki Babyna, ban san yadda zan misalta miki ba, ban san yadda zan fada miki ba” “Hajiya Ramatu tace kar na dade” Da sauri ya daga daga jikina ya juyo da ni ya rike kunkuruna. “Ta san kin zo?” Na gyada masa kai sai ya shafa kansa da dayan hannunsa. “Kai Amman Amina wawuya ce” Kumatuna ya sumbata da saman hancina sannan ya ce min. “Wuce ki je” Yana ba ni hanya na fara sauri kamar an biyoni har tashi faduwa nai. Da hawaye na shiga gidan ban san da hawayen ba sai da Amina ta tambayi abunda na ke yi wa kuka sannan na tuna da zaman hawayen a fuskata, saurin sharewa nai na dan turo baki kamar an min wani abu.    Har muka kwanta a dakin da Hajiya Ramatu ta bamu ni da Amina ban daina jin jikina na rawa ba, ina ta mamakin abunda Aliyu yai min sai kyamar bakina na ke saboda halshen daya saka min a ciki daman da na je alwalar isha'i sai da nai ta wanke bakin da amma ban daina jin kyama ba.    Washe gari muna gama sallah asuba Aliyu ya kira Amina a waya ta ba ni, ni kuma da na karba sai na saka cewa komai. “Good morning Babyna batar kin tashi lafiya” “Lafiya kalau” “Mashallah, Amaryata mai tsada” Na ji kunya ta lullube ni kamar ina gansa. “Ki ci abinci ki koshi kin ji?” Na gyada kai ba tare da na amsa ba, sai ya ji yayi murmushi mai sauti. “I love you....” Ya fada kamar mai rada. Sannan ya kashe wayar, ni dai mamaki ya kasa barina gaba daya ka kasa yarda cewar Aliyu ne. Misalin takwas na safe a kawo mana abincin karyawa kala kusan uku ni dai dankalin kawai na ci na sha ruwan sanyi domin ko tea din ban ji ina shawa'awar sha ba. Ina kokarin cire tufafina na shiga wanka Amina ta miko min wayarta wai Momy ce. “Hello Momy ina kwana” “Lafiya kalau Aisha kin tashi lafiya” “Lafiya kalau” “Mashallah kina bukatar wani abun ne?” “Ana mana komai a nan” “Masha-Allah haka na ke so, sai anjima da dare za ku dawo gida kinji? Amman yanzu ba ri a akaiwa Nana waya ku gaisa” Na amsa da to, haka na rike wayar har aka kaiwa Nana ina jin muryarta sai na ji wani farinciki ya cika ni cikin far'a muka gaisa da ita sannan na mikawa Amina wayar. Kamar yadda Momy ta fada ban mu koma gida ba sai da dare na yi zaton direba zata aiko ya dauke mu ashe Hajiyar ce da kanta zata kai mu, bayan ko wace awa biyu sai Aliyu ya kira wayar Amina ya ce ta ba ni tun tana dauka tai magana har ta kai idan ya kira sai dai kawai ta dauka ta miko min, tambaya yake wai ko ina bukatar wani abun sai na ce aa sai ya tambaya na ci abinci na ce masa ce daga haka kuma sai yai shiru yana sauraren numfashi har an wani lokaci sannan ya kashe. Ko da muka shiga gidan babu kowa sai wata budurwa da kuma su Siyama da Husna da gudu suka zo suka tarbe ni Momy kuma na zaune saman kujera tana kallona fuskarta da murmushi. Zaunar da ni sukai suna ta rumguna suna ja min kumatu Husna na ce min Amarya. “To a kyale ta haka nan taje ta ga Mamanta haba” Momy  ta fada. Siyama ta rika hannuna. “Muje na rakanki” Sai muka fito tare da ita tana rike da hannuna ni dai har Siyamar kunyarta na ke ji balle kuma Momy, Nana ma da zanje gurinta sai ma soma jin kunya kamar ba zan iya zuwa ba. MOMY POV. ataa na ficewa daga falon ita da Siyama Momy ta mike tsaye tare da Hajiya Ramatu suka nufi dakinta, Hajiya Ramatu na mata ya gajiyar biki. “Alhamdulillah” Momy ta fada tana zaunawa saman gado Hajiya Ramatu kuma ta zauna a kujera. Sai da suka fara firar daurin aure da taron da akai wanda Momy bata sa ran za'ayi ba sannan Hajiya Ramatu ta ce. “Ai kowa yayi mamakin jin auren daga sama, amman dai sati na sama za a kai masa matarsa ko?” “Aa ba yanzu ba ai, yarinyar ma da yanzu ake son ta fara makaranta? An dai yi auren ne kawai saboda hankalin kowa ya kwanta kuma a san mijinta kin ga ba wani zancen wane na so wane na so” “A a Wallahi karku tauye masa hakki, yaushe rabon ma da a daurawa mutum aure kuma Amarya bata tare a ranar ba? Ai bar wannan yayi ko a kauye, balle wani diban shekaru a gida? Wane namijin zai daukar miki haka?” “Ai ya san da maganar karatun na ta tun ba yau ba” “to karatuna yana hana aure ne? Ai aure baya hana karatu kuma karatu be hana aure, tai karatu tana karkashin kularwarsa ai zai fi dadi saman da tana gidanku abun ai be ma burge ba, karki biyewa kowa ki bar mata ta tare dakin miji kar ma a ja abu da sauri” “Haba Hajiya komai fa ba a shirya ba” “Shiri yanzu wani wahala ne da shi? Lefe ne ko tana dakinsa zai iya mata, kayan daki kuma rana daya za a iya siyowa indai a kasar nan ne, sai dai dan gyara gida da fenti ko kuma ya koma sabon gidan Alhaji da ya gina a wurno road ba dole sai an tsaya gina wani ba” “Ai ni bana son ya raba musu gida da Rahma, kara dai ya hade su ya zauna da su guri daya” “Har kin tuna min da ita, wai ta ji an yi auren nan ne?” “Wallahi ban sani ba amman ba zata rasa ji ba tun da yan'uwanta ko matan abokan Aliyu su fada mata kin san tana dubai fa har yanzu” “Haba dan Allah ko dan wannan be isa ya saka ki bar ya tare da matarsa? Ai ko dan wannan haushin ya isa ya saka ki barta ta tare, zaman gida na me kuma? Yanzu zamanta a nan tashin hankalinsa ne fiye da ba a daura auren ba ma” “Hajiya yarinyar nan bata iya komai ba bata san komai ba ko girki bana jin ta iya, ga kuma karatun da take son yi” “Karatu ai ana yi a gidan miji ni ba da aurena nai HND ba? Yar wajena Sumayyah ma da aurenta har da yara hudu tai karatu, abinci kuma gobe idan za ki shirya abun karyawa sa a kira miki ita ki shirya komai a gabata ko kuma ki bata kina fada mata tana yi kamin satin nan da zata tare ta iya wani abun sauran ta koya a can, amman Wallahi karki yarda ta dade a gidan nan ina tabbatar miki ko sati biyu tai a gidan nan sai Aliyu ya fara nuna miki damuwarsa, kan Rahma ta dawo ma ai sai a barshi da matarsa ya tare tana zuwa ta tararda wata ba saboda haka akai auren ba?” Momy ta yi shiru tana nazarin maganganunta, ta san gaskiya Hajiya Ramatu ta fada ita kanta ta yi wannan tunanin amman bata son Ataa da Nana su ga kamar ta matsa musu ne. “To yanzu dai sai na ji ta bakin Mahaifiyar yarinyar idan ta yarda” “Ai yarda ma za tai wake son a daurawa dansa aure kuma ya zauna masa a guri? Wannan ai sai rashin kunya ta shiga ciki ma, kin ga yadda yake kiranta a waya dazun? Abun har Mamaki ya ba ni, karki takura masa Wallahi ki bar matarsa ta tare komai sai ta koya a can idan ma school din koyon abincin zai saka ta duk daya” Momy ta yi murmushin jindadi. “Zan duba Hajiya Ramatu, ko dan saboda Rahma ai ta tafi ta bar shi sai ta dawo ta tararda wata” “Shine Ai Allah dai ya basu zama lafiya ya hada kansu” “Amin” Cewar Momy tana mikewa tsaye ganin Hajiya Ramatu ma ta tashi. Sorry 🙏😑 *Z A K I -it's not free, pay 300 to 0314795884 Abubakar Gt bank, then send the evidence via 08036126660* Wani irin bakinciki ne ya cika mata zuciya, sai hararar wayar take kamar Aliyu a gabanta. “Wai ni Aliyu zai yi ma kishiya? Kiji fa” Muneera ta tabe baki. “Ai daman nasan za a rina, daman can ba ya fara gajiya da ke, gashi nan tun yanzu kin fara gani ai, kuma ya rasa da wacce zai hada ki kishi sai wannan yarinyar, ai Wallahi ki ma gode Allah daya saka ba ki ma garin ke ma ki kasar gaba daya zancen hakan ya fi ma” “Ai Wallahi daga nan ma gaba zan kara sai ya raina kansa da wannan kazamar sannan idan ya ga dama ya dawo ya bada hakuri na ko?” “Au komawa ma za ki yi?” “Muneera to ya na iya ina son mijina, kuma dan wata banza ta aureshi ai be kamata na kyaleta da shi ba” “Yanzu ha hada ki kishi da wata banza marar asali kuma yar aikin gidanki, ya hada ki kishi da talaka karamar yarinya kamar wannan be fada miki zai yi auren ba, sai da aka daura aure shi ma kuma ta hanyar kawayenki kika ji haba Rahma ki daina abu kamar so ya haukatar da ke mana, dan za ki kara aure sai ya wulakanta uwargidansa, daman ma zaman nan haka suke kin dai san iyakar wulakanci Bawan Allah nan na miki shi” Idon hawaye ya cika da kwalla, sai a yanzu take jin ba dadi domin dazun haushi kawai take ji amman a yanzu ta soma ganin rashin kyautarwa da Aliyu yai mata. “Ke daina damuwa ki manta da komai ki yi kiba ki mulmule yau ko rabuwa Aliyu yai da ke shi yai hasara, Daddynmu na can yana nema miki kodar da Aliyu ya kasa nema miki saboda ya gaji da ke, ashe aure zai yi, yanzu ko rabuwa yai da ke idan kika samu lafiya sai ki auri mai haihuwa shi kuma yaje can ya karata da amaryar” “Ko a mafarki ban taba zaton Aliyu zai min haka ba, ban tana taba tsammanin haka ba ko a mafarki” “Ai namiji ba shi da tabbas namiji dan kunama, hmmm ai karki tana yarda zai so ki ke kadai ke kadai ranki” “Na shiga uku Muneera, zuciyarta kamar zata narke na ke ji, i can't believe tun ina raye Aliyu zai hada ni da wata, Wallahi ko bayan raina ya auri wata be kyauta min irin soyayyar da mukai balle kuma yanzu da na ke raye, bayan kuma ya san lalurata, baya tsoron abunda zai same ni? A yanzu kenan baya gudun bacin raina? Ashe Aliyu zai iya min haka?” Wasu zafafan hawaye ne ke sauko mata kamar ba gobe. “Ni kishiya? Ni...?” “Ai namiji kenan, kadan daga halinsa kika gani” “Komai raba mu za mu yi kenan? Yanzu Aliyu ba nawa ba ne ni kadai kenan? Wayyo Allah ” Ta fada da hargagin kuka tana saukowa daga saman gadon ta fado kasa tana wani irin kuka. Muneera ta taso da sauri ta dawo kusa da ita “Yanzu akan wannan abun za ki saka kanki kuka?” “Ina son mijina Muneera ba zan iya ganinsa da wata ba, taya zan rayu da Aliyu shi kuma ya rayu da wata? Taya Aliyu zai min haka? Muneera haukacewa ce zan yi wayyo zuciyata na kasa yarda cewar Aliyu ya auri yarinyar nan” “Haba Rahma a hotel muke fa, hotel din ma ta dubai idan kina irin wannan ihun kina kuka ai sai su dauka wani abun su shigo” “Gida na ke so Muneera, gida zan koma Nigeria na ke so ki fadawa Yaya ya kai ni ya shirya mu koma gida, Muneera zan iya mutuwa” Ta fada tana kara narkewa tana wani irin kuka mai ban tausayi. Ita kadai ta san abunda take ji a yanzu ita kadai tasan yadda taje son Aliyu kuma yanzu ace ya hada son ta da na wata? “Mi na masa? Mi na masa Muneera? Mi yake damunsa? Anya kina ganin na cancanci irin wannan sakarya?” Kuka take sosai, tun Muneera na lallabata har ta gaji ta zuba mata ido kamin ta tashi zuwa dakin yayansu inda ya tare da matarsa, after zuwan Muneera da Rahma shi ma ya zo hutu shi da matarsa. Kusan shi yake kula da Muneera da Rahma a lokacin da ya zo garin. Duk yadda Muneera da Yayanta suka so ta kwantar da hankali ta manta da Aliyu ta zauna a nan sai ta kasa gaba daya ta fita daga hayyacinta sai kuka take ta rasa inda zata saka kanta. Sosai yayan nata ya ji haushi yadda take kuma ta tashi hankalinsa domin shi ma yana ganin Aliyu ya nuna musu rashin kunya da kuma tozarci domin shi ma a ganinsa abunda Aliyu yai be kyauta ba taya ma zai auri wata mace bayan matarsa ba lafiya tana a cikin halin da take bukatarsa a maimakon ya nuna mata kulawa sai ya nemi kara aure wannan ma ai abun kunya ne kuma abun kataici. Har daga Mommynta sai da ta kirata da kanta ta fada mata ta kwantar da hankali ta zaunawarta a Dubai ta huta amman ta kasa bawa zuciyarta hakuri, a dole suka fara shirya komawarta gida Nigerian a gobe ita da Muneera wacce ta rakota shi kan ba be shirya komawarsa yanzu ba domin be gama shakatawarsa ta matarsa ba. ATAA POV. Siyama na gana ina biye sai wata tafiya na ke kamar mai jin nauyin taka kasa, gaba daya kunyar Nana nake ji na kasa sukuni na kasa sakewa har muka shiga dakin da take. Siyama tai sallama ni kuma na kasa cewa komai sai na zauna kusa da kofa kaina a kasa, Siyama kuma tai dariya ta fice. Gyara zama nai na rike hannyena ina ta wasa da su a cikin gyalena. “Al-hamdulillah na gode da ya nuna min wannan ranar, yau rana ce mai cike da farinciki a gurina, ban tsammaci zuwanta a lokacin da na ke raye ba, kuma ban tsammanin zuwanta a nan kusa ba, amman sai ga shi komai ya zo ta yadda ban yi zato ba, na gode Allah da yasa ina da rai akai auren nan” Dagowa nai na kalleta sai na ga hawaye a idonta murmushi kuma a fuskarsa. Sake maida kaina nai kasa domin har lokacin kunya na ke ji ni irin kunyar da na ke daga lokacin da aka daura auren nan zuwa yau har mamaki take ba ni domin ban taba sanin ina da ita ba sai a yanzu. Bayan sallah isha'i Hajiya Ramatu ta shigo bangaren da muke ita da Momy suka gaisa da Nana sai Momy ta ce min na tashi na je part dinta za tai magana da Nana. Ni kuma na tashi na fice ban je part din nata ba na zauna a gurin da ake aje motoci na zauna ina ta tunani ni kadai, cikin kuwa har da tunanin Rahma, ko a wane hali take a yanzu ko kuma zata ji idan ta ci cewar Aliyu ya aure ni, Mama Fulani ma ya za tai na san dai ba zata taba so na ba, ita da Rahma kuma za su iya ci min mutunci ko goranta idan suka ganni wata kila ma har duka sai Rahma ta yi min tace na aure mata miji, ko tana Abujar ma ko tana nan oho. Haka nai ta kawo wacan ina ture wannan har na soma jin bachi a gurin, can kuma su ka fito daga bq din Momy na takawa a hankali tare da kawarta har suka iso gurin motar kawar tata, a lokacin ni kuma na mike tsaye da zimmar komawa Bq din sai Hajiya Ramatu ta rike baki. “Laa yanzu a nan kika zauna? Ba ki je falon Hajiya ba?” “Kunya ta ke ji daman na lura da takunta ai” Ni dai na wuce ban ce komai ba sai watsa na ke da yan yatsuna, lokacin da na shiga bq na yi zaton Nana zata fada min wani abun akan zuwan Momy gurinta amman bata ce min komai ba sai dai tana ta kallona tana murmushi. A katifa daya muka kwanta kamar yadda muka saba sai dai jin kunyarta be hanani shigewa bayanta nai bachina ba har gari ya waye. Misalin bakwai da yan mintuna Momy ta aiko Husna tana kirana, bata jira mun tafi tare ba ta juya ta fice. Ni kuma na mike tsaye na dauki Hijab dina ina kokarin sakawa Nana ta ce. “Kin yi dacen suruka indai abun ya bi haka za ki jidadin zama da ita” Na kalleta sai kuma na sauke idona kasa, kamar na tambaya abunda ya Momy ta zo yi jiya a nan sai kuma na dauke kaina na fice daga bq din, kamar jiya yau ma da kunya na shiga part dinta sai na samu tana zaune falo ita kadai tana kwaba fulawa. Har kasa na kai na gaisheta ta amsa min da murmushi a fuskarta. “Shiga kitchen akwai tarugu da albarsa ki gagga min zan shigo yanzu” Tashi nai na shiga kitchen din sai na samu tarugun ta albarsa a cikin roba an aje kasa ga kuma turmi a kusa, bude turmin nai na yanka albarsa na fara dakawa sannan na zuba ta rugun na dake su a tare, ina karewa tana shigowa sai ta aje fulawar ta kunna fanfon kitchen din ta wanke hannunta. “Hadewa kikai?” “Eh a tare na same su” “Eh ko a tare ne ai za ki iya rabawa saboda wani lokacin ba komai ake hadewa ba, wani abun baya son albasa da yawa wani kuma tarugun ne ba za a saka da yawa ba, shiyasa ake son rabawar, daga yau karki sake hadewa idan kina jajage kinji?” “To” Daga haka ta nuna min inda zan murda a jikin gas din sannan ta miko min wani abu mai dan tsawo ta nuna min inda zan matsa wuta ta fito na sai na saka a gas din cikin tsoro nai hakan sai ga gas din ya kama da karfi sai kuma ya nuna min gurin ragewa da kuma yadda zan daidaita wutar. Dayan ma sakawa tai na kunna da kai ta na dora ruwa a kai ta bani boya wacce aka gyara ta ce na zuba a ciki kuma na rufe, sannan ta littafamin yadda zan soya tarugun da albarsa da yadda zan zuba kwai idan ya soyu sannan ta fita ta bar min kitchen din. Sosai na maida hankali ina yin yadda ta ce sai dadi na ke ji yau zan yi girki irin na masu kudi da kaina, sai dai tsoron gas din na ke ina ganin kamar fashewa zai yi ko kuma ya ja ni idan ina matsawa kusa. “Tace na soya tarugun da albarsa idan ya soyu sai na rage wutar na fada kwai na kada na saka magi a ciki sannan na zuba kwai ciki kuma kar na motsa idan yayi sai na saka wannan katon cibin na juya shi kar na bari ta karye ko ta yamutse, idan ta yi tace na saka a wannan kular nai haka har sau...... ” Ban karasa ba fadar abunda ke bakina na ji an riga kunkuru an doro min kai a wuyana. “Mi kike hadawa?” Saurin janye jikina nai na juyi ina ta kyarma irin na tsoro. “Ina wuni?” “Ina kwana?” Ya fada yana jan kumatuna, sai nai kasa da kaina. Waiga yai ya kalli kofar kitchen din sannan ya saka hannunsa biyu ya rika fuskata ya sumbace saman lips dina. Sai yai saurin juyawa ya fice yana murmushi, wani irin kazanta na ji kamar na cire bakina gaba daya, da sauri na na zuba omon da ke kusa da fofon na wanke saman bakin nawa da shi ina ta jin kyankyami. Ina dagowa sai na ganshi yana kallona sai kuma kunyarsa ta rufe ni, murmushi yai ya karaso kusa da ni ya sake rika fuskana ina jin kamar na masa magana ko nai ihu sai kuma na kasa yi sai kunya na ke ji wannan karon na iya saman bakina ya sumbarta ba, bakinsa ya saka cikin nawa ya rika jan yawu bakina yana hadewa yana ta wasa da halshensa a cikin bakina daga karshe ya turo min yawunsa kuma ya kwanto da ni hannunsa wanda hakan ya cilasta ni hadewa. Rumtse ido nai ma matse hannuna da jikina ina kokarin kankamewa guri daya, a dole sake ni sai ya bude kofar bayan ya fita daga kitchen din. Kakarin amai na fara yi wai ko yawunsa da suka shiga bakina za su fito na mayesu ashe Aliyu kazami na musamman duk tsabbatarsa ta banza ce, taya ma zaka saka bakinka a cikin bakin wani har ku yi musanyar yawu, ni da bana iya cin abinci a saitin bakin da wani ya ci ma. Na fi karfin minti goma ina ta kakarin aman sai kyankyami na ke ji ina ta tofarda yawu, sannan Momy ta shigo, ita ce ta lura da tarugun ya wuyu har ya fara konewa ma ni ban kula ba. “Mi kike har yai haka?” Na yi shiru ina ta tunanin abunda na ke, sai ta rage wutan ta fasa kwai da kanta ta mika min na zuba, har muka yi breakfast din muka gama Aliyu be sake shigowa kitchen din ba, ni kuma ban daina tara yawu a bakina ina zubawa a gurin fanfan kitchen din ba sai na zuba ruwa dan bana son Momy ta gani. Bayan na gama ita ta gasa tai sauran sai muka dawo falo muka jera komai. A gurin jerawar ma sai da ta gwada min yadda zan yi da kuma yadda zan aje komai a muhallinsa. Sannan ta zuba mana na mu ni da Nana ta ba ni, sai da zan wuce sannan na lura da Aliyu da ke zaune saman cushion yana danna wayarsa kamar ba shi ne yai min abunda yai min dazun ba. “Aisha kun gaisa?” Momy ta kirani sannan ta fada kamin na amsa ya dago kansa ya kalleni fuska. “Aa” “To idan kika ganshi ki rika gaishe shi hakan na da kyau kinji, kuma kamin ki karya ki wanke bakinki da brush” “To ina kwana” “Lafiya kalau” Ya amsa min fuskarsa babu murmushi ko wasa kamar ba shi ba. Ni kuma na fice ina ta masa kallon abunda yai min dazun. Ko da na isa part din wato bq na samu Nana na share saman balcony din saurin aje abincin hannuna nai na karbi sharar nakarasa, sai ta koma cikin daki ta zauna. Bayan na gama na je ma sameta na dauko abun karyawa na aje mata na shiga na wanke bakina kamar yadda Momy ta fada sannan na zo muka karya. “Ina jin kamar be dace ace har an miki aure Hajiya na zancen tarewarki a sati mai zuwa kuma ace yan'uwana da yan'uwan mahaifinki, ina jin kamar hakan be dace ba, kuma ina jin babu dadi idan na tuna da haka sai dai babu yadda zan yi” Bayan mun gama cin abincin take min wannan maganar, gabana ne ya fadi. “Tarewa ta sati mai zuwa Nana?” “Haka ta roka ita da matar da suka zo jiya, kuma ta ce idan na amince zata fadawa Mahaifin Aliyu sun fada min sun dauke nauyin komai, za su yi duk abunda ya dace, kuma za a hada miki kayan sakawarki wasu tun a nan wasu kuma sai kinje can Saboda kurewar lokaci, tace ba za ayi wani hidima ba amman tana son ta shirya yar walima saboda addu'a” Kuka na fara yi a take. “Karatuna fa? Yanzu kenan? Barin zuwa makarantar zan yi? Kuma bokan ma ba za a a saka ni ba?” “aa zancen karatunki tace yana nan za ki cigaba da karatunki ko bayan aure” “Aa nana ni ban yarda ba Wallahi bana so, ma fasa auren gaba daya Wallahi ba zan yarda ba, ni ba zan iya zaman da shi ba, wayyo Nana dan Allah karki bari na tare yanzu....” Shine abunda na ke fada ina rikon hannunta domin har ga Allah na tsorota da wani zaman aure a yanzu, yo ya ma zan yi zaman? Me ake cewa ya tsare tsaren suke ni na zan iya ba, ga wannan kazantar da yake min na san idan ina can sai ya sake min ita, karatuna ma lalacewa zai yi. Babu abunda Nana take sai kallo da fuskar tausayi domin kukan ba na wasa na ke ba. “Na riga na karba mata ba zan iya canjawa a yanzu ba, Allah yasa hakan shi ya fi alheri” Kara fadawa nai jikinta na fashe da kuka ina ta goga mata jikina kamar wata yarinya karama, bata ce min komai ba bayan hawayen da take har nai kuka na gama na tashi dan kaina na shiga bandakin na wanke fuskarta na saka uniform dina na tafi makarantar islamiya kasancewar ranar Lahadi ce ana zuwa da safe. Sai dai ban sake da kowa ba duk wanda ya kalleni ya san ina cikin damuwa domin har ga Allah bana son tarewar gaba daya ma sai na ji auren ya fita a raina. Da shabiyun rana aka tashe mu na dawo gida kamar wata marar lafiya, abincin rana kawai na ci Momy ta aiko wai nai wanka za mu fita, sai na shiga nai wanka na shirya a cikin daya daga rigunan da Aliyu ya siyo min a ranar da yaje da ni shopping. Amina aka kawo ta zo ta kirani muka shiga nota tare muka dauki hanyar gidan Zara mai lalle kalar fatata ta duba ta bani wasu abubuwan ta ce wannan na rika shafawa a jikina idan zan kwanta wannan kuma idan zan shiga da kamar minti goma haka, ni dai ji kawai na ke ba dan ina da niyar yi ba, daga ranar ban sake zuwa makarantar islamiya ba ban kuma sake saka Aliyu a idona ba, idan dare yayi sai Momy ta aiko min da fruits na sha, bayan kwana uku a gidan ta mayar da ni gurin wata kanwarta dake Abuja road, a can akai ta cusa min wasu abubuwa da na ke hadewa daker idan na gama na shiga bandaki nai kukana son raina na fito, duk na kasa sakewa a gidan lokaci zuwa lokaci Amina da Siyama da Husna suke zuwa su dubani, da dare fruit ake ba ni kamar yadda Momy take min a can sa safe kuma ba a bari na karya daabu mai nauyi da na ci kadan sai ace na barta haka a bani kaza mai magani da daci na ci, gashi tsoron matar na ke domin na lura ita ba kamar Momy ba ce sam bata wasa da yara balle ta sake da su, ba kuma wulakanci ba irin halin nan na dattijai. Kullum sai an kaini gurin Zara ta gyada min jiki, ta shafa min turare na jiki da na kai da kuma na tsiguno, sannan ta ba ni ruwan magani ta ce nai wanka idan ta gama min dilka ni kaina a yanzu ina jin dadin jikina domin fatar jikin har wani sheki take tayi laushi sosai fiye da da, gashin kaina kuwa kamar ba nawa ba, domin kullum cikin shafa masa mai take tana gyara shi, ita kanta yabon kyauna take gaba daya na koma kamar ba ni ba, domin kuwa na fi da kyau da haske duk wani datti na fuskata da jikina sai da aka kawarda shi. Wata kabila ce ta zo ta auna ni ko'ina na jiki sai da ta auna ta sannan ta tafi, haka na rika kwana a gidan kullum idan na yi marmarin ganin Nana sai da a kira min ita a waya shi ma kuma idan Siyama ta zo ko Amina ko kuma Momy ta kira, a gidan matar idan zata hada abunda be kai kmya kawo ba ko wani abu mai nauyi ba sai ta kirani ta nuna min ta tambaye ni na gane, ko ban gane ba cewa na ke na ge saboda kawai a wuce gurin, sai dai kullum sai na sha kukan dare ni kadai ba tare da kowa ya sani ba. ALIYU POV. Sai da ta wuce sannan ya mike ya nufi dinning yana fadin. “Tare kuka shirya abun karyawar ne?” “Eh wai ina dan koya mata ne kamin taje can ta koya gaba daya” Yayi shiru be ce komai ba har ya zauna ya bude abinci ya zubawa kansa ya soma ci yana ta tunanin abunda yai ma Ataa a dazu sai murmushi yake a zuciyarsa. “Aliyu yarinyarnan tana son karatu sosai fa” Da dago ya kalli Momy. “Na sani shiyasa na shigar da ita islamiya ai, kuma bokon ma zan saka nan gaba In-Sha-Allah” “Ina jin tsoro kar aurenku ya saka karatunta tarwatsewa” “Saboda me? As long as zatai zaman aure ai zan barta tai karatunta, ba ni da matsala da wannan amman Momy..... ” Sai kuma yai shiru ya kasa karasawa. Momy ta shiga zubawa Daddyn abincinsa tana tambayarsa. “Amman me?” “Tsawon wane lokaci zata dauka a gida tana karatun?” “Karatu yana da lokaci ne?” “Na yi magana da Daddynka jiya saboda Hajiya Ramatu ta kawo wata shawara har ta saka ni dole sai da naje bq nai magana da Nana ita kuma ta amince ta ce mana ba matsala, da na fadawa Daddynka sai yace shi babu ruwanshi shawara ta mu ce, kuma na kira babbar Yayarku after sallah asuba na fada mata komai ita ta bani shawara makamanciyar wacce Hajiya Ramatu ta ba ni” Da dago tana ta kallonta, gabansa na dan faduwa irin na tsoron nan idan ba wani abun za a bullo da shi ba, wata kila ace ya kai Ataa wata makarantar boko a Abuja ko kasar waje ko kuma ya barta gida har nan da wani lokaci mai tsawo wanda yake jin cewar ba zai iya haka ba. “Wani abun ne?” Sai da Momy ta gama warewa Daddyn nasa abun karyarwa sannan ta ce. “Wai Mun yanke shawarar Ataa ta tare dakinta next week Saturday” Wani irin dadi da mamaki da annashuwa da farinciki Aliyu ya ji lokaci daya, amman yai kokarin dannewa saboda kar Momy ta ga haukarsa ko rashin kunyarsa, yayi murmushin dake nuna jindadinsa amman ya boye duk wani jindadin na ainahi a cikin ruhinsa. “Amman Momy ita ta yarda?” “Aisha ai bata da matsala duk inda aka bi da ita bi za tai, Nana kuma t amince har ma godiya tai mana jin cewar an dauke mata komai” “Masha-Allah Allah ya tabbatar da alheri” “Amin sai ka fara shirye shirye tun a yanzu” Momy ta fada sannan ta dauki kayan abincin ta fice, wani irin murmushi Aliyu yai ya girgiza hannunsa ya shafa kansa abincin ma sai ya kasa ci. Tun daga lokacin ya fara shirye shirye kamar yadda Momy ta fada masa, kudi ya cire mai yawa ya bawa wata yayar Momy yar kasuwa ta siyoma Ataa expensive clothes da tsarkoki masu kyau da tsada shoe dinta ma abun kallo ne, kusan kala talatin aka mata nata na sakawa wai na yanzu da kuma na kwaliyar amarci kamin a dinka mata na lefe idan komai ya laba hankali ya kwanta zai mata cikakken lefe domin yana son ya mayarda ita mutum ita ta zama tana fita da shiga irin ta yayan manya. Bayan gidan da suka zauna d Rahma yana da wani gidan dabam mai kyau da tsare, wanda ya so ya aje Ataa a ciki ita kuma Rahma ya barta a wacan ma'ana ya raba musu gida saboda gudun fitina sai Momy ta hana ta saka Daddyn ya ba shi dayan gidansa mai part uku da ke unguwar koko road. Sabon fenti aka yi ma gidan duk kuwa da kasancewar ba a taba shigarsa ba, saka kara kawata shi aka gyara wasu abubuwan, sannan Momy tai order wasu furnitures daga Kaduna masu tsada da kyau aka kawo aka zuba a dayan bangaren na Ataa gaba daya furnitures din bangrenta fafare ne tun daga dago har kujeru da duk wani abu na kwaliyar daki, gurin curtains din ne kawai akai musu surki da ja da sai kuma carpet din shi ma ja, after two days da kawo furnitures aka saka Electronics da wasu abubuwan na kawata gida. Kayan kitchen kuma wata mai siyarda da kayan kitchen aka bawa kwangila da shirya komai on Friday aka saka. Ba Aliyu kadai ba, Momy m da yan'uwanta da Daddy da Abbah sun yi ma Ataa hidima sosai gurin gyara komai na gida. Sai dai duk wannan farinciki da jindadadi Ataa zata tare da Aliyu yake idan ya tuna cewar Babu Mama Fulani za ayi sai ya ji babu dadi, gashi tun lokacin da abun ya faru ta daina daukar wayarsa balle kuma ita ta kirashi da kanta Momy ma idan ta kira bata dagawa, sai dai ya kira Maryam ko. Rukaiyah ya tambayi lafiyarta. Kamar yadda Momy ta tsara ranar Saturday akai walima, ba a yi wani taro ba domin ba kowa da kowa Momy ta gayyato ba, saboda kurewar lokaci wasu ma jin abun na Momy ne yasa suka zo ba tare da an gayyoto su din ba, wani abun mamaki har da Maryam da Rukaiya da kuma yayan Ammy, wanda Momy take sa ka ran Abbah ne ya turo su da kansa, domin Mama Fulani dai fushi take ba zata taba cewa su zo ba, ko da yake wani lokacin Mama Fulani ta kan yi wani abun dan hada kan zuri'ar ta da kuma yayanta. Sosai Momy tai farinciki da ganinsu kuma ta jidadin zuwan na su. ATAA. POV. Ban kara tabbatar da cewar da gaske ne ba, sai da maga ana ta hidimar bikin, tun ranar laraba aka saka nai wa ka da ruwan lalle mai ja sosai, ranar da ta kama jumma aka zo aka kara gyara min gashina har gida, ba kitso aka min ba sai dai an gyara min shi yadda na ke jindadin zamansa a kaina. Lallen ma dan ubansu aka min mai kyau gaske, tun da nake a rayuwata ban taba yin lallae ba sai yau ashe haka yake kyau a fatata farin kafata dana hannuna ya fito fes lallen mai ja ya fito fes, domin ja ne kawai aka min da shi babu digon baki ko daya. Ranar assabar na tashi da wani azababben ciwon kai saboda na wuni na kuma kwana ina kuka da tunanin. Da yamma aka sake saka ni nai wani wankan wata mai kwaliyar ta zo ta shirya ni tai min fentin nan na kanti sai na fito kamar ba ni ba, dogon hancin nan nawa sai ya kara fitowa kowa cewar yake na yi kyau ni dai nawa idone kawai zuciyata kuma cike da kuka. A mota mai kyau aka saka ni aka tafi da ni gidan Momy a can na tararda taro har an fara walimar ma, a cikin mutanen da suka halarta da su Yayan Mama Fulani da Ammy Maryam da Rukaiya har bana son hada ido da su saboda harata da suke. Duk wani wa'axi na Malamar ban ji ko daya ba, I hawaye kawai nake har kwaliyar tawa ta hoda ta soma gogewa, na sha hotuna sosai. Kamin Momy ta saka a sake maida ni gudin Kanwar tata Hajiya Mairo sai dai wannan karon tare da duka yayanta muka tafi da kuma wasu bakin fuska da ban sani ba. Ta ba ni abinci amman na kasa ci ruwa ma kasa sha nai sai gani nake kamar mafarki na ke. Bayan na gama sallah isha'i wata mai kwaliyar ba wacan ba ta sake zuwa ta gyara ni na saka wasu tufafin lace ne ash color mai kyau da ja mayafi sai kuma ta kalmin suma kala daya da gyalena sarkar kuma irin wannan ce mai ruwan gol wata kila ma gol din ne ban gane ba. A gidan Momy aka sake dawowa da ni tare da yan matan dake tare da ni aka kai ni gurin Nana wai ta min huduba sai aka fita aka bar ni daga ni sai ita, riketa nai na fashe da kuka ji nake kamar idan na tafi na tafi kenan ba dawowa. Ita bata iya ce min komai sai kuka take har wata yar'uwar Daddy ta shigo zata fita da ni sai na rike Nana gam ina kuka kamar yadda ita ma take yi tana rike da hannuna. “Aure ai ya gaji haka, dan Allah ku yi hakuri sai kace wandanda akai wa mutuwa? Haba dai” Shine abunda mutane suke ta fada ganin irin yadda ni da Nana muke ta kuka sosai, babu wanda ya san abunda na ke ji sai ni yau zan rabu da Nana wai wani aure zan yi auren da sai a yanzu na ke jin nadamar amincewa da Aliyu da nai da na sani na ce ban shirya auren kowa ba sai na zauna ni na Nana mu yi ta rayuwarmu. Batan fitowa da ni bangaren Nana aka kai ni Gurin Momy dakin na cike da mutane a haka tai min nasiha sai na rike hannunta ina ta girgiza mata kai ina kuka ita ma kanta sai dai ta yi hawayen. Daker aka fito da ni aka saka ni a motar ina da kallon bq din Nana na tsaye jikin windows tana kallona ita da wasu yan'uwana Momy wata kila hakuri suke ba ta, a gidan baya aka sani ni tare da wasu mayan mata sauran yan matan kuma suka shiga sauran motocin, aka dauki hanya da ki hanyar da ban san wace unguwa ce ba domin kaina a kasa yake ina kuka har mutanen da ke cikin moyar suka soma tsarguwa da ni. Mun dade muna tafiyar sannan muna iso wani gida da ban san ina ne ba jin ana guda yasa gabana faduwa kuma na kara rushewa da kuka. Wata matar ce da ba zan iya shaidar fuskarta ba ke rike da hannuna tana nutsawa da ni a cikin gidan har muka isa falon da ke ta kamshin turare sannan muka wuce uwar daga ma'ana bedroom nan dai kamshi ke tashi da kuma mutane a ciki da ba xa su fi mutum biyar ba bayan falon da ma da akwai wasu a nan. A tsakiyar gadon aka zauna da ni sannan aka fesa min wani turaren aka kara gyara min mayafina yadda zai sauko min da kyau. Sai da dattijawan cikin suka min addu'a kuma suka min huduba akan zaman aure hakuri yi na yi ba ri na ba ri da kuma toshe kunnu akan dukan abunda zan ji ko na gani.   Sannan suka tafi aka barni da yan mata masu kokarin bude mayafina su ga fuskata ni ko har lokacin hawaye na ke, ina jin wani yanayi da ban taba jin kaina a ciki ba, hakika ban san aure ba, ban san miye aure ba balle abubuwan da suke cikinsa, amman iina jin darajata ta karu na bar kulawar Nana da tarbiyarta na koma gurin ta Aliyu kamar yadda Momy tai min huduba. Wata sabuwar rayuwarce zan fara fuskanta wata kila mai dadi ce ko akasin haka, wata kila mai sauki ce ko kishiyarta, wata kila kuma na samu duka biyun wato dadi da daci sauki da kuma wahala.    Bana iya gane lokacin da aka shigo da Aliyu hayaniyar maza kawai na ji a dakin wasu na zolarsa, ban daga kaina a cikin mayafin na kalle ko su waye da waye a abokansa ba, amman nasan sun hausa mutum biyar kuma ba za su sama da mutu goma ba, baki gado ya zauna yana ga kamshin turarensa mai dadin shaka. Nasir ne ya fara yi mana nasiha sannan wani abokinsa ya dora sai kuma suka rufe da addu'a tare dayi mana fatar samun zaman lafiya kwanciyar hankali da kuma zuri'a ta gari. Da dai daya suka fara fita sannan sauran suka fice har da matan sai ya tashi ya raka abokansa, ina jin lokacin da motacinsu suka tashi suka bar cikin gidan sai kuma na ji yana jan kofar falon alamar rufewa yake.   Da zai dawo dakin sai da yai sallama sannan ya shigo, ni kuma na kasa amsawa har lokacin kaina na kasa ina ta wasa da yatsun hannuna, a inda ya zauna dazu ya sake zaunawa. “Amarya.... ” Sai na ji wata kunyar ta sake rufe. Kara hawowa yai saman gadon ya miko hannunsa ya bude mayafin da ke kaina ya dora shi a bayana yana murmushi sai kuma ya saka hannun na sa ya dago kaina sai na lumshe ido. “Godiya ga Ubangijin da ya mallaka min wannan halittar ta inda ban yi zato ba, tsarki ya tabbata a gareka ya Allah” Ya fada sannan ya Hura min iska a saman idona da suke kulle. “Bude idonki ki kalli Masoyinki, bude idonki ki kalli mijinki na har abada” A hankali ya bude ido sai na sauke su a cikin na shi, ta cikin kwayar ido muke kallon juna ni da shi wani irin sako yake aika ta cikin idon da ban wayanci na minene ba, ni ko hawaye sai aikinsu suke a idona. Wani lallausan murmushi yai min ya kai hannunsa a fuska ta share min hawayena sannan ya kara matsowa kusa da ji yai min masauki a kirjinsa, rumgume ni yai kamar wata yar baby sai juyani yake a hankali irin yadda ake yi ma yara. Ni kuwa na samu damar yin hawaye iya son raina, sai na ji dumin bakinsa a goshina, ya sumbace ni ba normal sumbata yai min ba yadda yake dora lips dinsa a goshin nawa ya sotsa ya dauke kamar zai janyo jinin goshin nawa ya sha ne, sai kara matseni yake a kirjinsa kamar wani zai kwace masa ni, a take jikina ya fara rawa domin ba a tana rumgume irin yadda ya rumgume ni ba. A hankali ya dago fuskata shi kuma ya duko da fuskarsa ya sumbaci tsinin hancina, ya sumbanci kumatuna sai kuma ya sake komawa ya sumbaci goashina kamin ya hade bakina da na sake rumtse ido ina jin wani irin kyankyami da kuma faduwar gaba a lokaci daya. A hankali yake shan lebena na kasa sai kuma ya yai sama da bakinsa ya sha na saman. ALIYU POV. Tana da soft and sweet lips Aliyu mutum ne mai son kiss sosai, ji yake kamar yana shan wata madara a bakinta, har Lumashe ido yake yana budewa, sai ya fi jindadi da kwanciyar da zakin lips sumbatarar a yanzu fiye da yadda ya sumbace ta a last time a kitchen wata kila saboda ya fi bukatatar a yanzu ne ko kuma saboda ya fi kwanciyar hankali da sakewa ne. Ya dauki tsawon lokaci a haka kamar ita da shi za su dauwama a haka ne sannan ya sake ta ya dago yana bude idonsa da su sauya kala ya jingina goshinsa saman nata yana ta kallon idonta da ke rufe sai shima ya rufe idon yana sauke numfashin a hankali. “Taso mu yi alwala mu yi sallah” Ya fada yana bude idonsa, kokarin dagawa tai daga jikinsa sai yai saurin bude idon ya rigata sauka daga kan gadon ya cire babbar rigarsa ya aje gefe ya bude mata bandakin. Takawa ta fara yi a hankali yana ta kallon fuakarta kamar zai hadeta har ta karaso kusa da shi ta shiga bandakin. Shiga yai ya kunna tap din ya tara hannunta ya wanke mata ya tara hannunsa ruwan suka taru ya kai mata a baki ta kuskure sannan ya shaka mata hancin da kansa, ya wanke mata fuska, hannu har ta kai ga shafar kai, ya kwakula mata kunnenta sai kuma ya dagota ya tara kafarta ya ya wanke mata dayar ma yai mata haka sannan ya sauketa ya sumbaci samman gashinta. Shi kan sai da ya tabbatace wani bangare na jikinsa sannan yai alwalar ya fito ya sameta bakin gado zaune. Carpet biyu ya shimfida musu tashi tana gaban tata sannan ya fita daga dakin zuwa dakinta wardrobe ya bude inda aka zuba mata duka kayanta yai ta ya mutsa har ya samu hijab ya dauko mata ya dawo dakinsa, fa kansa ya saka mata Hijab din sannan ya matso da ita ya kawo ta gurin carpet din ya tsayar da ita kamar wacce aka ce masa bata gani, har sallah ma ji yakd kamar yai mata domin yau son ta a zuciyarsa na musamman ne. Sai da ya fara ikama sannan ya kabbata. Raka biyu sukai suka sallame sannan ya daga hannunsa yai ma Allah godiya yai musu addu'a ya shafa ita ma ya shafa sai ya juyo ya kama goshinta ya karanta addu'a sai ya sumbaci goshin, kamin ya saka hannunsa ya cire mata hijab. Tashi yai yaje ya dauko wata leda da ke gefen gado ya bude mata gassashiyar kaza ce da madara irin fresh milk din nan mai kyau. Da kanshi yaje ya dauko cup daya ya zuba mata milk din sannan ya dauki kazar ya kai mata a baki sai ta kawarda fuska. “Na koshi” Be ce mata komai ba ya mika hannunsa janyota ta dawo kusa da shi ya kwantar da ita a jikinsa sai ta lafe kamar wata kanwa, dibar naman kazar yake a baki yana taunawa kadan sai ya dago kanta ya hade bakinsu ya tura mata naman a baki, a dole take taunawa ta hade kamin ta hade ya tauna wani ya sake hade bakinsu ya tura mata a ciki. Madararce kawai ya daga kofin ya kai mata a baki ba tare daya gunda ta ba, sai ta bude baki kadan kamar wacce bata saba cin abinci ba tana sha a hankali. Wacce ta zubo mata a gefen baki sai ya saka halshensa ya lashe da kuma wacce ta tsaya a saman lebenta. “Kin koshi?” Ta gyada kai a hankali sai wani nutse kai take kasa, gaba daya ta zama wata solobuyu duk yadda ya juyata yi take. Tashi hai ya shiga bandaki ya wanke hannunsa sannan ya fito falo ya nufa ya kashe wuta da tv da aka bar musu sake ya dawo dakin. “Ta so” Ya mika mata hannunsa, dagowa tai tana kallon hannun sannan ta mika masa nata mai zanen lalle sai da mike tsaye sai ya sumbaci hannun ya juyo da shi ciki ya sumbaci tsakiyar sai halshensa yake sakawa yana wasa da tsakiyar hannunta. Kamin ya kai hannunsa ya fara shafa gashin kanta yana shinshinawa. Jin ta hade yawu da karfi ta matsa baya yasa ya kalleta sai ya dagata ya kwantar da ita bakin gado ya risina daga gurin kafafunwa ya fara shafa lalleta fa farar kafarta mai taushi wacce ta sha dilka. Saman kafar ya fara kissing sai kuma kasan kafar sannan ya saka babban yatsansa a bakinsa ya fara tsusa kamar yaro ya samu sweet. Saurin fisge kafar tai ta tashi zaune sai shi ma ya tashi tsaye yana tande baki. “Hau gado ki kwanta” “Aa kasa zan kwanta” Matsawo yai kusa da ita ya kai hannunsa ya ja lips dinta. “Kin taba ganin Amarya ta kwanta kasa ranar aurenta?” Ya fada mata a kunne kamar mai rada sai ya saka mata halshensa a kunneta ya fara wasa da kunnen nata yana tsosa a take ta soma jin ba dadi, sai ta fisge kunnenta daga bakinsa ta hau saman gadon ta kwanta dan dole ta. Wani kasaitaccen murmushi yai ya nufi wutar dakin ya kashe sai ya rage sauran bed side lamp kawai, ya hau samna gadon ya kwanta ta bayanta sannan ya kashe bed side lamp din, gudu ya mamaye dakin gaba daya, baka hango haske sai ta gurin curtains din windows din dakin shi ma ba sosai ba domin curtains din masu kauri ne sosai. Bayanta ya fara kissing yana ta yamutsa gashin kanta na baya har gurin kiyar kanta yake kissing, saurin juyowa tai dan ya daina ashe bakinta ne abunda ya fi bukata a yanzu, a cikin hudun ya hade bakinsu yana sani irin jan numfashinsa yana fitarwa ita numfashin take ja ta fitar sai dai yana da banbanci da na shi nata na wahala ne da tsoro shi kuma na jindadi ne da samun abunda ka dade kana muradi. Jin wasansa zai fi karfinta yasa ta fashe masa da kuka, tun yana kissing din bakinta har ya sauko gurin wuyanta ya nemi masauki a kirjinta, duk inda ya rika a jikintan riko yake mata bana wasa ba, tun yana mata a hankali tana yin shiru tana amsa sakonsa dan dole har ya fara fin karfin kwakwalwarta, daman can haka yake idan yai marmari baya wasa da wannan babin. “Aliyu dan Allah kai hakuri ka bari kaji Yaya Aliyu, dan Allah” Juyar da ita yai ya kifar da ita yai karasa cire abunda ya rage a jikinta, tana ta ta yawo da hannunsa yadda yake so bayanta kamin ya juyo da ita. Jin yana kokarin kaiwa inda take jin ba zata taba iya barin kowa ya kai a nan ba yasa ta fara kuka kamar daman can ta tanadi kukanta ne kawai dan domin irin wannan ranar ta yau. Addu'a ya karanta sannan ya fara yi da kamar hankali kamin ya birkice mata, babu kalar kukan da batai ba tun tana kiran dan Allah dan Annabi har ta koma hada shi da Momy da Daddy, ta kira Nana can kuma ta koma tana hada shi da Mama Fulani amman sam baya ma jin ihunta balle har tausayinta ya shiga ransa, shi be tana tausayin mace a wannan bangaren ba. Sai da yai kwanka sannan ya kwanta bayanta ya saka ta a kirjinsa ta bayanta ya rumgume yana jin sani irin son ta da kaunarta na masa yawu a zuciya da jiki da duka wani guri da jini da numfashi yake shiga. Kiran sallah asuba ya tashe shi sauka yai daga kan gadon ya kunna wutar dakin wanda hakan yasa Ataa ga bude idonta ta kalleshi, zuwa yai ya yaye blanket din jikinta sai ga babu komai a jikinta, daukarta yai ya shiga da ita bathroom ya hada mata ruwa mai zafi ya saka a ciki, kana ganinta kasan bata da wani karfi ko kuzari a jikinta, ba zancen kunya ko wani abun take a yanzu ba, ta wani zama kamar ba ita ba. A cikin ruwan ya barta sai da yaje masallaci yai sallah ya dawo sannan ya sake lekowa bathroom din sai ya sameta a cikin tana lumshe ido alamar bachin take ji har yanzu. Wani lausayinta ne ya kama shi ya san abunda yai ko Rahma tana kuka da shi wani lokacin balle kuma Ataa. Gashin kanta ya fara rikawa ya tufke mata shi guri daya sannan ya tambayeta. “Kin iya wankan tsarki?” Ta gyada masa kai. “Waya koya miki?” Ta daga hannu sama domin magana ma a yanzu wahala take mata. “Mama (Nana)” Ta gyada kai sai yai murmushi. Da taimakonsa tai wankan ta ya fito da ita da kansa domin shi kanshi yana jin ba zata iya tafiya da kafafuwanta a lokacin, babu tufafin a jikinta ya fito da ita ta zauna bakin gado tana ta natse kafafuwanta saboda azabar da take ji a guri har jin take kamar wani kwaro na mata motsi a gurin, duk inda wata halitta nata na jiki na musamman yake zafi yake mata kama daga kirjinta har zuwa kunkurunta da take jin kamar karewa zai yi idan ta mike tsaye, kasanta ma zafi yake mata na fitar hankali sai hade yawu take tana bin Aliyu da kallo duk inda yai har ya fita yaje ya dauko mata abaya ya saka mata da hijab gaba daya ta koma kamar wata yar baby. Shi ya shimfida mata carpet ya zauna ya zuba mata ido yana ta kallonta har tai sallah ta gama sannan yaje ya dauko kur'ane ya zauna kusa da ita ya kwantar da kanta a cinyarsa ya bude kur'anin ya soma karantawa da kira'a mai dadin sauraro. Tun tana jin kirara tasa har bachi yai gaba da ita, ya dade yana karatun sai da Rana ta fito sannan ya daga kanta a hankali ya aje kasa sai ta bude ido ta tashi zaune, maida qur'anen yai a muhallinsa sannan ya dawo ya miko mata hannunsa. “Ta so” Bata fuska tai ya tana kokarin gashewa da kuka, domin a tunaninta abunda yai mata jiya zai kara mata a yanzun ma. Dayan hannunsa ya sake miko mata. “Ta so mana baby na” Ta mika hannayen duka biyu ya mikar da ita tsaye sai ya tura jikinta zuwa gurin gadon bachinsa. Cire mata Hijab yai ya aje gefe ya rikata ya kwnatar saman gadon sannan shi ma ya kwanta yana kissing gaban goshinta. “Hug me” Ya fada jin ta yi shiru yasa ya sake cewa. “Rumgume ni sai ki yi bachinki babu abunda zan miki” Ba musu ta rumgumeshi ta shigar da kanta jikinsa ya runtse ido. Kwakwalwarta na tariyo mata abunda ya faru jiya, shi kanshi abunda ya faru yake tunani wani irin farincikin ne da nishadi a zuciyarsa da ruhinsa, ya sameta fiye da yadda ya za ci zai sameta ya jita fiye da yadda yake tunani a duk ma'aunin da zai aunata a zuciyarsa yanzu zai ga kamar ya rage mata matsayi ne. Saman kanta ya dinga kissing kamar wani mahaukaci ya kuma rumgumeta tsantsan a kirjinsa kamar yadda ta rumgume shi saboda kunyarsa da ta taso mata yanzu. Na su yi bachin minti talatin zuwa arba'in ba door bell din falon ya fara kara alamar akwai mutum a waje. Bude ido yai a hankali ya sauka daga kan gadon ya sumbace kumatunta sannan ya gyara mata zanen ya lulllube abarsa da kyau sannan ya fito falo bude kofar ma a hankali yai kar kararta ta tashe ta. Siyama ya gani da wasu cousins sisters dinsa su hudu suna dauke da abinci. “Ina kwana yaya? Momy ta ce akawo muku abun karya” Amsa nata da dan murmushi a fuskarsa kamar yadda yai ma sauran sannan ha basu guri suka isa cikin fakon suka aje abincin a muhallinsa suka juyo suka fito da sauri kamar wadanda ake kora. Kulle kofar yai ya dawo dakin da ya bar Ataa sai ya same ta zaune tana hawaye. Saman gadon ya hau ya raba kafafuwansa biyu ya saka nata a tsakiya ya matse fuskarta tana jin saukar numfashinsa yana jin nata. “Minene?” Kasa amsawa tai sai baya baya take har ya kwanta jikin gadon yai mata rumfa da kirjinsa, ya sumbaci hancinta kumatunta da kuma goshinta sannan ya sauka ya daga kan gadon, tufafin jikinsa ya cire a gurin which is normal for him indai a gaban matarsa ne zai iya kuma yana bukatar yin hakan a gabanta domin ta soma sabawa da halayensa sun yanzu, wanda hakan yasa ta saurin kawarda fuskarta. Yana gamawa da kansa ya janyota ya shiga rabata da gown din jikinta ita ko sai rokonsa take a zatonta yar jiya za a sake yi. “Wanka za mu yi sannan mu ci abincin karyarwa” Ya fada yana daukar tawul daya ya daura sannan ya miko mata dayan, kasa daura tawul din tai saboda ta nade a cikin blanket shi kan be bi ta kanta ba sai gai kamar ma be lura da abunda tai ba. Sai da ya fara shiga ya hada musu ruwan wankan sannan ya fito yana daure da tawul din ya bude blanket din ya fito da ita ta daga ta sama cak ya nufi toilet. A tare sukai wankan ba dan ranta ya so ba sai dan dolenta brush din ma sabo daya ya fasa musu sai da ya fara yi sannan ya wanke mata nata bakin, ya saba yi ma mace komai, dafa mata abinci, wanka, brush, kawo mata abincin da ba mai nauyi ba, bata ruwa and so on kuma be tana gazawa ko gajiyawa ba domin a gurinsa matarsa yar lelensa ce kuma yar gata ba yar wahala ba, Rahma ma yai mata balle Ataa da yake ganin yarinya ce ba komai ta sani ba ko ta iya. Tawul daya ya rage a bandakin dan haka ya daura mata shi ya fito a haka ha nufi wardrobe dinta ya bude ya fara saka boxer da vest sannan ya nufi madubi ya shafa abubuwan daya saba shafawa tare da tutaren jiki sai kuma ya dawo ya saka shadda da sauran abubuwa. Ko da ya juyo tana zaune bakin gadon ka ta a kasa, dan karamin tawul din a jikinta, fita yai zuwa dakinta ha dauko mata wasu riga da wando na yadi marar nauyi ya saka mata da kansa. Sannan ya juya ya tara mata bayansa. “Hau muje falo mu karya” ATAA POV. “Zan iya tafiya da kaina” Na fada ina dan turo baki sai ya ce. “Bana son kina min gardama idan na ce ki yi abu ki yi kawai, ko ba a fada miki duk abunda na saka ki yi ba?” “An ce” Na fada daker. “Then hau” Ya fada yana hadawa da turanci, a dole na hau bayansa ya mike tsaye da ni kamar wata yar baby, sai da ya fara tafiya sai ya saki hannunsa a dole na kankanme shi da kafafuwa da hannuna gudun faduwa kaina kuma a bayansa ma lafe kamar maciji, dan Murmushi na ji yayi mai sauti sannan ya nufo falon da ni. Har gurin Dinning ya kai ni sai ya sauke ni tsaye yaja kujera ya zauna ya nuna min cinyarsa. “Zauna a nan” “A nan?” Na kara tambaya dan tabbatarwa. Be ce min komai sai kallona yake wanda kallon ke ba ni ma'anar zaman a dole na zauna ina jin kamar na fashe da kuka domin na lura sam Aliyu ba shi da kunya gaba daya ni ga ni nake kamar ba shi ne ba. A saman ciyarsa ya gyara min ya sumbance ni sannan ya mika hannu ya shiga zuba abincin ina saman jikinsa, a plate daya ya zuba mana abincin ya rika ba ni da hannunsa, sai da na koshi sannan ya umarce ni da shi ma na bashi, spoon na dauko zan saka na bashi sai ya girgiza min kai. “No na san da spoon na baki da hannu, da hannu na ke son ki ba ni, hakan na kara kauna sa soyayyah, kuma yana cire kyamar juna” Ya kamata yatsuna na saka na rika debowa ina kai masa a baki, idan na saka masa baki sai ya tsotse yatsun nawa tas sannan ya bari na fito da su, har da dan cizo na yake kadan da kamar keta sai yai dariya idan ya ga na bata fuska. Sai da na gama bashi abincin sai ya saka bakinshi a cikin nawa ya tsotsi bakina ya tura min yawunsa ya karbi nawa kamar yadda yai min a wacan karon da kuma jiya, yanzun ma daker na hade har ina runtse ido. “I love you so much” Ya fada yana rumgume sosai yana shafa bayana. Mun dade a haka sannan ya dago ni yana min murmushi kamar ba shi ba ya shafa gefen fuskata. “Ce I love you too” Na yi shiru sai ya sake maimaitawa still ban ce masa komai ba. Sai ya fara min kwakulkuli irin yadda ake yi ma yara duk yadda na so na daure na ki dariya kasawa nai a dole nai dariyar sai dai ba mai yawa ba. “Haba you look cute amman kin wani hade giran sama da kasa bana son ganin fuskarki a haka” Ban ce masa komai ba, sai ya zagaye hannayensa a jikina yana ta shinshinata kamar mai wani kanshi. *Khadeeja Candy* Bayan mun bar dinning ya ce na koma ciki na saka lace ko atamfa wai za a iya zuwa ganin Amarya. Tafiya na fara yi sai dai ba yadda na basa ba saboda zafin da na ke ji a kasana, a rabe nake tafiya kana gani kasan akwai abunda ya faru. “Oh no Baby u can't walk in front of others like this, ai sai inji kunya” Ban fahimci abunda ya fada min da farko ba sai a karshe na fahimci kalmarsa. Na bata fuska sosai kamar nai kuka har idona na cika da kwalla. Tasowa yai ya zo kusa da ni ya rumgume ni ta baya ya dora kansa saman kaina. “Oh Sorry Sweet Baby next ba zai miki haka ba, amman dai ba sai kinyi tafiya a gaban mutane ba, ki yi zamanki a daki” Jinsa kawai na ke amman ya za'ayi ace na zauna a daki na tsawon lokaci ba tare da na fita ko da dauko wani abu ba, ko kuma yin alwala “Bari na fita na samo miki wani abu a chemist ko za ki samu sauki” Ya fada yana sumbatar kunnena sannan ya saka hannunsa biyu ya dauke ni sai na rufe ido domin har ga Allah ina jin kunyarsa har yanzu wata kila ma wata kunyar sai gaba domin ni dai har yanzu mamakin abubuwan da suka faru na ke, ina ta ganin kamar ba gaske ba. Na yi zaton dakin da muka kwana zai kaini sai ya kaini wani dakin wanda ya fi wacan yaduwa da kwaliya kana ganin wannan kasan na mata ne tun daga furniture din har decorations din dakin. Saman gado ya sauke ni yana dariya ganin ya rufe ido. “Nan ne dakin ki Baby na, wacan dakina ne” Ban ce komai ba sai dai na bude ido na sauke su kasa. Sai ya nufi wardrobe be ya bude kofofinsu gaba daya. “Wane kike so? Lace ko Atamfa ko material ko shadda?” Na yi shiru na kasa magana ni ban san abunda zan zaba ba ma. Sai ya dauko min wani farin yadi mai kyau sosai ya kawo min a maimakon ya ce na saka sai ya shiga kokarin cire rigan da wanda daya saka min dazun ha saka min wannan farin yadun da kansa. “Zan iya sakawa da kaina Aliyu” Na fada amman be saurare ni ba be kuma ce min komai ba, ina ji ina gani sai fa ya sake rabani da tufafin jikina ya saka min yadin ba sannan ya dauki dankwalin ya daura min akai irin daurin dankwalin nan na tsofafi ya fito min da gashin kaina ta kasan dankwalin, kumatuna ya sumbata na dama da hadu ya sa saka babban yatsasa ya share min hawaye sannan ya fice daga dakin ba tare da ya ce min komai ba. Kwanata nai a bakin gadon na fara kuka kamar wacce akai wa mutuwa, tsanina da Allah indai haka auren yake irin wannan zabar da na sha jiya to ya yafe auren, domin na lura zama da Aliyu ba dadi zan ji ba duk kuwa da na lura yana kulawa da ni sosai amman bana son wasu abubuwan da halayensa, sai kuma tunanin Nana ya dawo min sabo wata kila tana can ita ma tana kuka kamar domin nasan zatai kadaice kamar yadda nima zan yi a nan. Ina cikin kukan na ji shigowarsa falon kasancewar kofar tana kara idan an bude tsabanin idan za a fita ba a jin kararta. Yana shigowa ya dagoni yana ta kallon fuskata. “Minene?” Sai nai shiru nai kasa da kaina na daina kukan mai sauti sai dai hawaye na min zuba har yanzu. Hannusa ya saka ya rika lips dina ha dan za kadan har sai da na ji zafi. “Na lura kina da jin kai ko baby? Maganara rowarta kike ko kuma shagwa6a ce yai miki yawa?” Nan ma shiru ban ce komai ba sai turo bakina da nai, murmushi yai ya bude maganin ya debo min ruwa na sha sannan ya rumgume ni a kirjinsa yana ta sauke ajiyar zuciya a hankali yana shafa bayana. “Kin zo min ta inda ban yi zato ba, ban tana tsammani son wata mace bayan Rahma ba, hasali ma ban taba tunanin karin aure bayan auren Rahma ba, duk kuwa da ba alkawari na mata cewar ba zan kara wata ba, sai dan haka tsarin rayuwata yake saboda bana son hayani, kuma ina jin cewar kamar mutum daya kawai zuciyata zata so matar da na aura da farko ko da kuwa ba Rahma ba ce, abun ban sani ba ashe Allah ya rubuto min aurenki a cikin rayuwata kaddarar mu daban dabam amman zama zai hada mu ta inda ni da ke ba mu yi tsammani ba, I'm sorry to say na tsani talaka ina ganinsa marar amfani kuma kaskantace ashe wata rana zan so talaka har nai rayuwa da shi, amman wannan duk a da ne, haduwa ta dake ta saka na sauya, ta saka na yi abubuwan da ban taba sammanin aikata su ba, kin dasa min wasu abubuwan da ban taba tunanin zamansu a zuciyata ba, ina matukar jin tausayinki, ina matukar kaunarki, ina da buri sama miki ingantacciyar rayuwar da kika rasa shekaru da dama da suka wuce, zan kula da ke baby zan baki duka hakkinki, kuma zan dauki nauyin ko wace lalura ko matsala ta ki, zan share ko wane kukanki, ki daina damun kanki a kaina, yadda na ke a waje ba haka na ke a cikin gida ba, i promise you za ki ji dadin zama da ni, kuma zan jira har lokacin da za ki kaunace ni” Lafewa nai a kirjinsa maganganunsa sun min dadi kuma sun kwantar min da hankali duk kuwa da hankalin nawa be kwanta gaba daya ba. “Zaka bar ni nai karatu?” Na tambaya a shagwabe domin al'adata ce yin magana a haka ko da a haban Nana ne. “Yes amman yanzu ina son idan mun yi sati daya a nan za mu je wata kasar honeymoon idan mun dawo kuma Abuja za mu zauna” Na dago da sauri na kalleshi. “Wata kasa? Jirki zaka shiga kenan? Minene Honeymoon din?” “Za mu shiga dai jirgi dai, ni da ke zamu je ai” Murmushi nai domin ina jindadin jirgi zan shiga kuma na je wata kasar, abunda ban taba kawowa araina ba. “Amman dan Allah muje da Nana ita ma tana son zuwa wata kasar, zata jidadi idan muka je da ita kuma nima zan jidadi idan da ita ne” Murmushi yai ya sumbaci hancina. “That's why i love you wautarki n burge ni, honeymoon yawon shakatawa ne tsakanin masoya mata da miji, kin ga ai ba zai yiyu na je tare da ita ba, amman idan an kwana biyu za mu iya shirya mata nata tafiyar dabam, a lokacin muna Abuja ita sai ta tafi” “Abuja? Gurin Mama fulani” Na tambaya ina turo baki. “No gidana dai, amman zamu iya kaiwa Mama Fulani ziyara, kuma mostly idan ina Abuja idan bana gidana ina gidan Mama Fulani” “Gidanka inda Rahma?” “Ai bangarenta dabam na ki dabam” “Ni bana son ta...” Na fada kai tsaye ina turo baki domin har ga Allah bana son ta bana kaunarta ko ganinta ma bana son yi ba kuma tsoronta na ke ba, domin ban ga abunda take da shi zan ji tsoronta ta ba, tsanarta na ke ji a duk lokacin da na tuna da cewar kodar Nana tana jikknta sai na ji kamar na shake mata wuya ta mutu gaba daya, ga rashin tausayi da imani irin na ta da na ubanta. Bakin nawa ya sumbata kamin ya tura min halshensa ya tsotse yawun bakinsa tas sannan ya cire bakinsa. “Ni dai bana ana son zama Abuja nan” “Tsoro kike ji?” “a a bana so dai” “I'm sorry dear zama Abuja ya zame min dole a can na ke aiki ai kin sani, kamfanin Daddy ne dole ni zan kula da shi tunda ni ya dora akai, i trust Nasir zai iya komai amman abubuwa zasu iya masa yawa, and Daddy ma ba zai jidadi na ace na dawo nan na zauna a nan na bar shi a can, amman idan mun dawo mun tare a Abuja zan saka ki makaranta a can boko da islamiya” Wani irin dadi ne ya lullube ni a take ya bayyana a fuskata. Sai shi ma yai kasaitaccen murmushi ya shafa fuskata ya kwantar da kaina jikin tafin hannunsa yama jan hancina. “I love you” Shi kan na san ma'anarsa sai nai saurin kulle idona na dauke kaina daga hannunsa sai ya saka hannunsa wai dole sai ya bude min ido ni kuma na cige shi a gefen hannun da gaganta dan ya kyaleni, jin yayi raki yasa na bude idon ina kallonsa sai yai min gwalo. Mikewa yai tsaye jin ana knocked kofar falon. “Maybe kin fara baki azo ganin Amaryata” Ya fada yana kashe min ido. Binsa nai da kallon har ya fice, gaba daya gani na ke kamar ba Aliyu da ba ne, mai hade rai, ya ba ta fuska, dakawa mutane tsawa, kyamar mutane, wulakanta mutane, kin son far'a da murmushi. gaba daya ya koma kamar ba shi ba, tun daga lokacin daya fara min maganar cewar na amince da shi ha fara bani mamaki kuma yana sake min balle kuma jiya da yau gaba daya ya gama chaja min kwakwalwa. Ranar mutane wuni sukai suna shigowa gidan kama daga yan'uwnsa na gurin Daddy da kuma yan'uwan Momy ina gane hakan ta haryar nuna min da Amina take tana fada min ko wace ga alakarta da Aliyu da kuma sunana da yadda zan kirata ko ta kirani, dukansu suna da far'a da sakewa manyan cikinsu duk wace ta zo sai ta min kyau na wani abun ci ko sakawa ko kuma kudi. Duk wani abu da aka ci a gidan daga gurin Momy ya fito domin ita ta saka aka dafa a can aka aiko mana, haka ma dare ta sake aiko mana wani sai da yan matan suka ci sannan suka fara shirin tafiya ni dai na saka sakewa da kowa sai dai hakan be hanani jin ba dadin tafiyar da za su yi su bar ni. Amina ta miko min wayarta “Anty Aisha ga Mamaki za ku gaisa” Da sauri na karba na kai kunne, yadda na ji muryar Nana cikin far'a yasa na jidadi kuma na cire kuncin kadaicin da nake tunanin tana fama da shi a can. Da yaren buzanci muka gaisa ta tambayeni lafiya da komai ni ma na tambayeta sannan ta kara min huduba akan zamantakewar aure sai mu kai sallama. Cilasta ni Amina tai sai da nai waka ta zaba min tufafin da zan saka tai min kwaliya ta saka min turare kuma ta taurare gidan sannan suka tafi daga baya ita da wata kawarda ta suka rage. ALIYU POV. Lokacin da ya bude gidan yar arba da Amina da wasu cousins sisters dinsa sai ya gaisa da su kamar yadda ha saba fuskarsa ba yabo ba fallasa sam ba zaka ganshi a nan kace shine ya gama yi ma Ataa magana mai dadi yana mata wasa da dariya ba. Fita yai wanda hakan ya ba su damar shiga cikin falon. A jikin motarsa ya tsaya ya ciro wayarsa daga aljihunsa ya kira number Rahma dake kasar waje, ba zai kira dan wani abun ba face tambayar lafiyarta, ya san yanayin ciwonta shiyasa wani lokacin baya biye mata and he know tana kishinsa sosai mai son ka kuma shine zai yi kishinka, kiran da zai mata bana bukatar ta dawo gidansa ba ne ko neman shiryawa da ita sai dan yasan hakkinta yana kansa ya kula da lafiya. Kasa samun number yai wanda hakan ke nufin ko dai ta bar kasar zuwa wata kasar ko kuma tana daina amfani da line. Number na gida Nigeria ya kira sai ya samu ta shiga abunda be tsammaci zai samu number ba. Ringing tai har ta katse ba ta dauka ba. Sai kawai ya saka wayar aljihu ya bude motarsa ya shiga yana jin ransa fes son Ataa na ratsa ko'ina na jikinsa sai murmushi yake idan ya tuna abunda ya faru jiya, gaskiya Momy ta yi tunani mai kyau da ta kawo shawarar auren Ataa shi sai yanzu yake jin dadin maganganun da Mommyn Rahma ta fada nata wata kila da bata fada mata ba, da yanzu ba tai wannan tunanin ba. Gida na nufa ya fara gaisawa da Momy da wasu baki da suke nan sannan ya shiga bq ba ko kunya ya gaishe da Nana sai wani kasa yake da kai yana murmushi, sai dai yana fitowa bq din ya hade rai kamar yadda ya ke ya shiga motarsa ya dauki hanyar gidansa dake sama road gurin Nasir da wasu abokansa da suka zo daga Abuja rako ango dakin Amarya jiya. Babu kalar zolayar da basu masa ba, ba sai dai yai murmushi kamar yadda ya saba amman baya ce musu komai da ma Nasir ne kadai zai iya fada masa wata magana dan yai dariya ko kuma ya rama zolayarsa. Sun zagaya a cikin garin sokoto wasu guraren da ba su sani ni ba kasancewar bakin garin damin su basu samu zuwa daurin auren ba shiyasa Nasir ya fada musu tarewar ango suka zo. Sai yamma lis sannan suka nufi airport jirginsu be tashi ba sai karfe 8:00pm dai-dai na dare. Daga airport Aliyu ya nufo wani shago da ake siyarda kayan makulashe yai leda biyu sannan ya dawo gida. Be tsaya knocked ko danna bell din kofar ya ya saka keys din hannunsa ya bude kofar ya tura a hankali ya shiga. Falo ya aje ledar sannan ya nufi dakin da Amaryarsa take fuskarsa dauke da murmushi. Yana shiga tai saurin dagowa ta kalleshi kamar a tsorace take, ga jan bakinta yaja gefe da alama goge shi tai, ido ta sakar masa har ya karaso kusa da ita sannan ya zauna bakin gadon yana yawo da idonsa akan fuskarsa. “Ba ni nai kwalkiyar ba Amina ce tai min” Ta fada tana dan turo baki abunda ke matukar burgeshi. Murmushi yai yasan tana jin kunya ne kar ya ce ta yi kwaliya saboda shi, hannu ya saka yana goge mata gefen bakin da janbaki ya taba. “Miye laifi dan kin yi kwaliya saboda ni? Mijinki ne ni fa, kuma gaisuwa ya kamata ki fara min kamin ki ki ce komai” “Ina wuni” Ta fada kamar an mata dole sai ya kama yatsun hannunga yana murzawa a hankali ya kai bakinshi ya sumbaci nata. “Lafiya kalau kina lafiya Babyna” Sai tai shiru ya saka hannu ya ciro wayarsa. “A kira miki Nana?” “Mun gaisa da ita ai dazun da wayar Amina” “kin yi sallah isha'i?” Ta gyada kai. “Good girl, ta so muje falo na siyo miki abubuwa ma su zaƙi ki ci” Mikewa gai tsaye sai yaki sakin hannunta har sai ta juyo ta kalleshi sannan ya mike tsaye ya daga kafadarta yana kokarin saka mata hannu cikin riga daga saman rigar. Saurin matsawa tai. “Ni dai ban ci” “Kina son abunda na siyo miki fa, kaza ce da kayan sanyi da na dadi” ATAA POV. Lake kafada nai na juya baya ina turo baki domin na gano manufarsa tunda har yai niyar saka min hannu a riga to yar jiya za'ayi ai ko jiya kazar ya ba ni yai min wayo yau har da wani kayan zaƙi da dadi. Cak na ji an daukeni sama an juya da ni cikin dakin sannan ya sauke ni ya juyo da ni ina fuskantarta. “Ba zan fasa miki abunda nai miki jiya ba, kin san babu wanda za a kawo wa amarya irin ki ya kwana da ke gado daya kuma a tashi lafiya kalau, bayan kuma ni har na dandana na ji” Haka ya fada min kai tsaye ba ko kunya, ina jin haka na fashe masa da kuka domin har ga Allah bana son abun nan sosai nake kukan ina bayyana kiyayyata akan abunda ya faru jiya sai kawai na ga yana dariya har da daukata a wayarsa wai kuka ma ya amsa kyau, ganin kamar ba zai dauki abun da gaske ba yasa na daina bude muryar na cigaba da hawaye kawai. Mayarda wayar yai aljihu ya kama kukuruna ya rike ya sumbaci hawayen nawa sannan ya saka bakinshi cikin nawa ya tsotse komai har sai da na fara jin halshena na tardewa da nasa tukuna ya cire bakinsa yana wani irin lumashe ido kamar wanda ya sha wani abu mai dadi. “Idan na saka bakina cikin na ki abunda na ke miki shi za ki min, idan kina haka za ki jidadi kuma halshenki ba zai tarde da nawa ba” Ha fada yana lakatar hanci. Ni dai ban ce masa komai ba bayan kasa da nai da kaina, sannan ya rika hannuna muka nufi palon. Duk yadda ya so na sake jiki na ci abunda ya siyo min sai na kasa musamman da yake fada min wai biyansa zan yi har da wani kashe min ido yake irin na yan iska. Bam dauka da gaske yake na har sai da muka je kwanciyar babu yadda ban mada dagiya akan ni dakina zan kwana ba amman ya hana ni ina ji ina gani ya dauke ni ya kai dakinsa, a tare mukai wani wanka ni dai idona a rufe har muka fito ina hawaye saboda tunanin da tsoron abunda zai faru shi kuma ko a jiki ni ina ta mamaki shi baya ma jin zafi da ciwo kamar yadda na ke ji ne. Kara ma jiya da tufafi na kwanta yau kan hana ni saka tufafin yai ina fashewa da kuka sai yaji jikinsa yana rarrashina da barana yana taba wani gurin ma jikina da na fahimci abun da gaske ni sai na fara kokuwa da shi domin yau na ji sakewa sama da jiya da nake jin kamar mafarki na ke. Ban tsira ba, ban kuma fasa kuka kamar jiya ba, ban k fasa rokonsa ba, ban fasa jin zafi kamar jiya ba, shi ma kuma be fasa yin kwatakwancin abunda yai jiya ba. Kamar jiya yau ma shi ya hada min ruwan dumi na gasa jikina da su har bana son fita ciki saboda dadin da suka min, yau ma a cinyarsa nai bachi bayan gama sallah azuba yai karatunsa na kur'ane. Momy ta sake aiko mana da abun karyawa kamar yadda tai mana jiya, sai da ya wanke min bakina ya wanke na shi sannan muka fito falo karyawa har lokacin idona a kumbure suke saboda kukan da na shaka jiya. A yau kasa muka kauna tsabanin jiya da muka karya akan dinning, shi yai ta ba ni abinci sai da na ci na koshi sannan ya saka ni na bashi ni kuma na ki sai ya saka chokali mai yatsu yana cikana da shi, tun ina dauri har na kai na unkura na tashi na basho guri sai ya rike ni. “Yi hakuri Baby na, indai dan abun jiya ne ba za a sake ba” “Har a bada?” Na tambaya da sauri ina kallonsa. “Har gobe dai” Na bani amsa yana shafa gashin kaina. “Ni dai anjima zan je gurin Nana” Be ce min komai ya yana ta wasa da gashin nawa da dayan hannunsa dayan kuma yana cin abincin da shi. “Babyna, Mama bata tana fada miki labarin wani nata ba? Like familynta Mahaifiyarta ko mahaifinta” Shiru nai ina tunanin fada masa ko a a, idan na fada masa wane amfani zai masa wata kila ma Nana ba zata jidadin bayyana hakan ba, wata kila am kimarta da mutuncin su zube a idonsa, ni dai ban ce masa komai ba shi kuma be sake tambaya ta ba har ya gama cin abinci. RAHMA POV. Kowa yana tsakar gidana yana hada hada da far'a ana kai kawo da murnar lefen kanwarta Amra da aka kawo amman ita tana a daki zaune hannunta rike da waya tana kallon kiran Aliyu ya da shigo wayarta har ya katse gaba daga ba tana aikinta na kuka. Babu abunda zuciyarta ke raya mata sai cewar Aliyu ya kwana da wata mace ba ita ba, ashe zai iya haka? Taya zata raba komai da da wata watan ma Ataa? Yanzu duk irin soyayya da dawainiyar da yake nuna mata haka zai yi ma Ataa? “Aliyu baka kyauta min ba, kuma na san wannan duk kullin Momy ne da Mama Fulani saboda basa kaunata... Daman na san za su saka auren ko dan abunda Mommy tai bata kyauta min ba.... ” Bata karaba Ikram ta shigo dakin daukar ragowar Naman ragon da aka tarbi yan kawo lefe da shi, ganin tana kuka yasa ta zauna kusa da ita ta dafa ta. “Rahma lafiya?” “Kin san abunda yake damuna Ikram, mi na rasa da Aliyu zai wulakanta ni yai aure? Auren ma wacce tai mana aiki domin kawai ya kara nuna duniya ba ni da muhimmanci a gurinsa?” Ta fada cikin kuka kamar wata karamar yarinyar abun sai cinta yake a rai. “Haba Rahma, ai Wallahi Aliyu yayi hakurin zama da ke na lokaci be yi aure ba, duk kuwa da irin ciwon da kike fama da shi, yanzu kuma ai ke kika jawa kanki haka kawai daga dan abu kadan kin kwaso kin dawo gida kuma mahaifiyarsa ta zo bikonki Mommy ta ci mata mutunci har da mata gorin danta baya haihuwa bayan kuma ita ga yarta nan ba lafiya amman ya zauna ke a haka, ai wallahi indai ba wawa ba ne dole yai aure ya shareki, kin ga ko wannan tafiyar da kikai zuwa dubai ba da izininsa kika yi ba, kuma kin san hakan be dace ba, kin barshi can shi kadai kamar marar galihu kuma yanzu yayi aure har ki yi korafi ai Wallahi ki gode Allah da be aiko miki da takadar sakinki ba” Rahma ta kalleta da sauri. “Ya kira ni yanzu bam dauka ba, ko sakina zai yi? Na shiga uku Wallahi ina son mijina Ikram” Ta kara fashewa da kuka. “Indai kina son mijinki ki shirya tsakaninki da shi, kuma ki tattara ki koma dakinki ki zauna lafiya da abokiyar zamanki” “Ba zan taba zaman lafiya da wace ta aure min miji ba, kuma yar aiki gidana yar talaka marar daraja, ba zan taba bari ta haki iska mai kyau a gidan nan ba” Ta fada tana jin cewar zata iya hana Ataa sukuni da walwala idan har ta koma gidan, domin ta san Aliyu yana sonta ba zai hana ta yin komai ba ciki kuwa har da musgunawa Ataa, wata kila ma baya son Ataa ya aureta ne kawai saboda Momy da Mama Fulani, ce mata da yai wacce zata kula da shi ya aura ta ina Ataa zata iya kula da shi yarinya karama kuma wacce bata waye ba yar talakawa wacce bata leka ko'ina ba balle har ta san yadda duniyar take ta san soyayya. Share hawayenta tai tana jin cewar ta samu mafita domin idan har ta koma gidan sai ta kori Ataa. “Dan Allah ta so muje kowa yana can ana murna, bikin da za ayi Daddy yace mai gidansa ma zai zo” “Wanda yake kasar Agadez?” “Shi fa ya ce ya fada masa da wuri kuma yana ganin zai zo saboda yace zai zo ganinki be samu zuwa ba ga kuma gobarar da aka masa be aiko ba kuma be zo ya masa jaje ba, sannan yanzu kuma ga bikin Amra yana ganin zai zo domin akwai ma wani kamfani da aka siya masa a Abuja da jigawa idan ya zo duk zai kai ziyara ya can” Rahma ta kara share hawayenta ta mike ta bi yar'uwarta suka fita tare zuwa falon gida na inda kowa ke zaune ana wasa da dariya da kuma duba lefen da aka kawo. *Z A K I -it's not free, pay 300 to 0314795884 Abubakar Gt bank, then send the evidence via 08036126660* *Khadeeja Candy* Mama Fulani na zaune falo waya a kunnenta tana magana a hankali ita da kawarta Hajiya Zainab Arzika, Muhseen ya shigo falon fuskarsa dauke da murmushi wayarsa kuma a hannunsa yana kallon wayar har ua zauna, gaba daya hankalinsa yana gurin wayar.   Sai da Mama Fulani ta gama wayar sannan ta kalleshi. “Ya akai Muhseen” “Lfy kalau, Mama duba min yarinyar nan tana da kyau kuwa?” Ya mikawa Mama Fulani wayar da ke rike a hannunsa mai dauke da hoton wata kyakkyawar yarinya. “Kai mashallah amman tana da kyau Wallahi wacece?” “Surukarki ce” Ya fada da murmushi a fuskarsa. “To ai ba girin girin ba tai mai ba na saurin murna saboda ban san ko yar wacece ba kar a min na Ataa?” Ambatar Ataa da Mama Fulani tai yasa ran Muhseen ya dan bace domin baya son tuna a yanzu balle kuma jin suna ta. “Wannan fa yar bachi ce kuma mahaifine shine Shugaban ma'aikata” “Shugaban ma'aikata na nan Abuja ko na can bauchi?” “Nan Abuja” “Wow amman ka kyauta haba ni kan yanzu na ji magana, ina kuka hadu?” “A twitter muka hadu, har na je gidansu mun gaisa sau biyu ma” “Mashallah tana dai son ka ko?” “A yadda ta karbe ni kan ya nuna haka, Mama ai yana da wahala in shiga wani gurin ace ba a so na gaskiya” Mama Fulani ta yi murmushi. “Yanzu na ji batu za ka yi auren cire raini kuma auren da kai aure yanzu ka dawo cikin hayyacinka, Maryam Rukaiya ku fito ku ga kyakkyawa” Mama Fulani ta karasa tana kwala musu kira. Rukaiyah ce ta fito yayinda Maryam ta ke can cikin daki abun duniya ya isheta saboda baikon da akai ma Humaira, gashi ita ce babba, wadanda suke warin Rukaiya ma Barula da Zee ta san na gaba kadan tsayar da mijin za su yi a barsu su kadai ita da Rukaiya a gida sai kuma kanensu kanana Baby da Inteesar. Da far'a Rukaiya ta sauka domin daga jin yanayin kiran Mama Fulani ta san wani abun ne ya samu, kusa da Muhseen da ke murmushi ta zauna tun kan tai magana Mama Fulani ta mika mata wayar tana dariya. “Kin ga wacce yayanki ya dauko yar mutanen arziki” Rukaiya ta karba tana wara ido. “Wow amman wannan yarinyar akwai kyau ni kama na santa ma” “Ba za ki rasa saninta ba tana da mabiya da yawa a twitter” “Amman tana da kyau sosai gaskiya wane gari take?” “Bauchi amman a nan suke zama Abuja tare da Babanta” “Gaskiya Ya Muhseen ka dauko mai kyau” Murmushin jindadi yai shi dai yana son ace ya auri mace mai kyau kuma yana son ya auri mace da idan abokansa da kowa na shi ya ganta sai sun sara mishi akan kyauta inda za a rika maganarta a duk inda ta wuce. “Ita da Ataa wace ta fi kyau?” “Haba dai ka sawo wannan kazamar yarinyar, wannan ai ta fita cika da komai wannan fa babban budurwa ce Ataa kuma yarinya karama da ita kuma ita Ataa yar ba yar kowa ba ce wannan ko yar masu abun ce, wannan ma ai har ta fi Ataa kyau sai dai kawai ace ita hancinta ya fi na Ataa kauri shi ma dan Ataa tana yarinya ne” Wani irin dadi ne ya lullube Muhseen yana jin cewar yanzu kan yayi zabe kuma ba zai yarda ta subuce masa ba tunda har Mama Fulani tana sonta. “Daman can fa akwai mata masu kyau saboda ba ku dubawa ne shiyasa ba ku san da su ba, yanzu ba gashi ba, shi ma Aliyu da be yi sauri ba da ya hadu da mai kyau ai wacce ta fi Ataa” Mama Fulani ta fada. “Amman ina magana Amina? Ba Momy ta ce ta baka Amina ba?” Cewar Rukaiya tana kallonsa sai ya amsa mata kai tsaye. “Bana son ta ana zancen mata masu mahaukacin kyau kya sako min Amina?” “Aiko Amina na kyau Muhseen” Ya kalli Mama Fulani cikin wacce tai maganar. “Tana da kyau ai na sani, amman na irin wanda na ke so ba, ni na fi son mace mai kyau bala'i wacce kowa zai san na aura, wannan ma ba barinta zan yi ta dade ba kar wani yai min kwantar 6auna dan haka ku fara shiri tun yanzu, Mama kuma ki fadawa Abbah idan kun tattauna za mu yi can tsakaninmu” “Karka samu damuwa Muhseen In-Sha-Allah sai ta aureka, ko nawa ake kashewa za mu kashe mu aurota” Muhseen ya mike tsaye yana jindadin furucin Mama Fulani daman ya san zatai supporting dinsa tun da yar masu kudi ce, shi kuma ya samu kalar da yake so saboda tana da kyau shi daman kyau ne kawai abunda yake iya saka shi ya so mace. Ba ya jin zai dauki lokaci be yi auren ba kamar yadda ya fadawa Mama Fulani saboda ya cire haushi Aliyu ya nuna masa ya samu wacce yake so cikin kankanen lokaci kuma mai kyau kamar Ataa auren kece raini zai yi auren da zai amsa sunansa a garin Abuja. Rukaiya ta tabe baki tana kallon Mama Fulani. “Ai idan akwai irin wadannan kyawawan ba yadda za ayi maza su zo su ce suna son mu” “Kin ji ki da wata magana, ita Humaira kyau ta fi ku ne? Kuma ai kyawawa ne kuma ko ba a son dan kyau ba a so ku dan kudin ubanku” “Amman Mama irin yayan manyan amsu kudin nan ina ruwansu da kudin ubanmu? Ai suma cewa za su yi suna da kudinsu ko ubansu na su to miye abun so kenan?” “Ai wani dan ace yar wani ya aura mace ko bata da kyau zai aureta, balle ki da kyau na ku, ku kwantar da hankalinki kuma na ku yana nan zuwa In-Sha-Allah, dan Humaira ta samu au sauran suna nan su ba a musu baikon ba kuma Humaira ce kanwarsu” “Amman Mama kin ga Batula da Zainab fa yayan mutumen nan sun ce suna son su kin san ko ba abunda zai hana auren sai idan mazan ne suka fasa, azo a yi musu aure mu muna nan zaune” Rakaiya ta karasa tana buga kafa kasa tare da bata fuska kamar za tai kuka. “To laifin waye? Kullum kuna nan cikin gida ba fita ko yar kwarkwasar nan mai janyo hankali maza ba ku iya ba ai dole bakin jini yai muku yawa, ita wannan ba ta Twitter Muhseen ya fadu da ita ba? Ku da wani be hadu da ku ba? Amman kwaliya ma sai dai kawai ku shafa mai ba wani kwaliya” “Su ma ai ba kwaliyar suke ba Wallahi har mun fi su kwaliyar arziki, amman gashi nan duk sun samu kuma ko kamin wacan na nijar din su zo ai kowacce sun tana da samarinta amman mu babu ko daya” “To kwantar da hankalinki ai Abbah ku yace sarkin Agadaz zai zo ya duba kamfanin da kansa da wasu dabam da suke wani gurin kika sani idan suka zo ko wani ya ganku ya ce yana son ku, ku dai ku yi fata kawai Allah kawo shi lafiya kuma Allah ya saka su ce suna son ku kamar wannan family idan na samu ke ko maryam kuka shige ai shikenan na huta nikan tawa samu na hada surukanta da Sarkin Agadaz” Rukaiya ta yi shiru ba dan maganar Mama Fulani ta kwantar mata da hankali ba sai dan babu wani abun da zata iya yi idan ma sun zo ba lallai ne su ce suna son su ba domin wacan zuwan ma ai ba su ce ba. Ita da Maryam wannan rashin manemi ya ishesu sosai suna damuwa da wannan matsalar domin ta nan kawai Allah ya rage su, suna ta iyaye a rayu masu hali ga family ta ko'ina ga ilmi kyau nan ma gwargwado suna da shi amman sun rasa manemi daga ita har yar'uwarta Maryam, ko an fara zuwa sai mutum ba zai dawo ba idan kuma haduwar online ce ma ba za a zo ba. RAHMA POV. Tana zaune falon mahaifinta kanta a kasa sai rabon ido take tana sauraren irin amsar da za su bata. Ba Mommy kadai da take mace ba har Daddynta yau haushinta yake ji na abunda ta fada taya suna fafutukar nema mata lafiya suna fushi da Aliyu akan abunda yai mata yanzu zata zo musu da wani zancen wai Aliyu ya kirata ya ce ta dawo dakinta? “Idan ma da gaske ne, ai shi zai zo ya tafi da ke mana ba wai ya bugo miki waya ba, ke kike wahalar da kanki akansa shi yana can ya yi aure ya manta da ke ma” Mommy ta fada a hasale. “Ba kiji irin magiyar da yake min ba Mommy wannan yarinyar ya fada min hada shi Momy tai da ita saboda huce ta kaini yace min yanzu haka baya ma shiga dakinta, har da kukansa yana ta rikona na dawo” Haka ta tsara karyar ta murje ido kamar gaske. “Yana son ki dawo shine ba zai zo ya tafi da ke ba sai dai ki kai kanki? Wannan ai zubar da kimarki ne idan ma baki sani ba” “Wai ba zai zo ba saboda abunda kikai wa mahaifiyarsa tace idan ya zo nan sai ta tsaba masa, auren ma duk itace tai ita da Mama Fulani saboda huce takaici har wani cewa suke wai na shanye shi” “Ina kika ji?” “Shi ya fada min jiya da dare a waya mantawa ma nai ban yi recording ba, da kunya har da kukan shi Wallahi” Mommy ta nuna ta gatsanta. “Ke tun kamin a haife ni na san wayo, ba zaki koma ba Matukar ba shi ya zo bikinko ki kuma sai mana alkawarin wacan ba zata takura miki ba, dan ba za mu zuba miki ido ki mutu ba, idan ke ba ki son kanki mu da muka haife ki muna son ki” “Ai Wallahi wacan yarinyar har aiki ce aka kawo min shi ma ai ya fada, yace duk wani aiki na gidan ita zata rika yi, ni hutawa kawai yake son nai” “To mun ji tashi ki tafi” Haka ta taso cikin bakinciki rashin amincewa ta koma da iyayenta suka yi, yanzu kam bata san karyar da zata musu ba, sai dai ta kira Aliyu ta rokeshi akan ya yarda ya zo ya dauke ta idan ya ki zata ba shi hakuri ma, ita dai burinta kawai ta ganta a gida daya da Ataa yadda zata jidadij ci amata mutunci kuma kallon da kawayenta suke mata na mijinta yayi aure ya barta su daina shi kowa ya san cewa yar wanke wanke aka auro mata, ta san Aliyu ba zai hana ta ba, domin shi kanshi baya son talaka kuma ta san babu ta yadda zai iya zaman auren da Ataa balle har wata alaka ta hada su, tunanin sharing ma da gai na cewar abunda yake mata zai iya yi ma Ataa yanzu take jin cewar ta yi kuskure saboda Aliyu ba sa'an Ataa ne ba ko da wasa ba zai yarda ta zauna kusa da shi ba ma, a iya tunaninta a yanzu Ataa na can daki dabam shi kuma yana daki dabam, ko cewar da yai wacce zata kula da mijin kawai aka auro tana tunanin ya fada mata haka ne saboda ta ji haushi tunda ta tafi ta barshi. Ai da ta zumudin amarya yake da ba zai kirata ba, sai yanzu take jin bakinciki rashin daukar kiran da ba tai ba, wata kila ma hakuri zai bata kuma ya roki ta dawo dakinta ko kuma ya bukaci ta bashi dama ya zo ya tafi da ita, ta san irin rayuwar da suke da kuma yadda Aliyu yake da kyama da kin kula mata ba zai iya raba zuciyarsa da jikinsa wa mace biyu ba, mace ma kazama yar bara kuma yar aikin gidansa kamar Ataa. “Hahaha yarinyar za ki ci ubanki ba dai mijina kika aura ba? Kina yar talakanki kika jawa kanki wahala Wallahi sai kin yi kuka da idonki kuma kin gwammace ba a taba halittarki duniya ba” Ta fada yana shiga dakinta na da wanda ya kasance mallakin Muneera a yanzu, ita da Muneera suke sharing a yanzu. Gaban madubi ta zauna tana kallon kanta a madubi ta mika hannu ta dauki wayarta ta kira Aliyu, ringing biyu a na uku ya daga sai yai shiru yana jiran tai magana kamar yadda ya saba idan dai kai ka kirashi ba shi ya kiraka ba ko da ma shi ya kiraka idan uzurin naka ne kyalewa zai yi sai ka yi magana da kanka. “Aliyu” Ta fada a shagwabe tana tana wani cream dake gaban madubi. “Ka kira ni jiya” “Lafiyarki zan tambaya” “Ka damu da ni kenan? Amman ka auro wata” “Wata aba kanki take ba, ke ma kuma ba akanta kike ba, idan kina da wata maganar ki fada” Kasa cewa tai ya zo ya je da ita ko kuma yai hakuri tana son har sai shi da kansa ya bata hakuri ko kuma ya roketa ta dawo da kanta idan ma ba zai iya zuwa din ba. “Dear kina bukatar wani abun ne?” “Aliyu ba zaka ba ni hakuri ba? Na zaka ce komai a auren da kai ba?” “Ina nufin kina bukatar wani abun kamar na ci ko na sha ko wani abun daya shafi lafiyarki?” Ta ji haushi a take ta kashe wayarta tana buga kafa kasa, ta san halin mijinta da jin kai ai, ba zai bata hakuri ba tun da yana ganin shi ne da gaskiya, amman zata jira har nan da sati daya ko biyu idan ya be ce ta zo ba ko be biyota ba zata share shi, balle ma tasan yana yin hakan ne kawai dan ya bata haushi kamar yadda yake mata idan yana fushi da ita a gida, ta san Aliyu can't live without her shiyasa ya turo mahaifiyarsa ta bata hakuri ta koma wacan karon duk kuwa da ya san yana da gaskiya, yanzu ma saboda abunda Mommynta tai ne da yanzu ya sake aikowa ko kuma ya zo da kansa. ALIYU POV. ya sauke wayar, ya amsa wayar a gaban Ataa ne saboda Rahma ta kira shi kamar yadda zai iya amsawa wayar Ataa a gaban Rahma saboda dukansu matansa ne kuma wani uzurin zai iya sakawa wata ta kira, da dai ba daga daga cikinsu ba ne, sai kuma Momy ko Mama Fulani Daddy Abbah, bayansu sai ya ga dama yake daukar waya idan an kira ko da yana waje balle kuma yana tare da iyalansa. Aje wayar yai gefena yana kallon Ataa wacce ke ta motsi kamar bata jin dadin zaman, ta turo baki sai hawaye take a hankali. “Ba kya jinddin zaman ne?” “Zafi ni dai har yanzu” Ya san abunda take nufi sai kawai yai yar dariya, ya mike tsaye ya dauke ta ya nufi dakinsa da ita. “So kike a kara kenan?” “Wallahi baka da tausayi kai mugu ne” Ta fashe da kuka. “Ni ne mugun?” Ya tambaya yana cige baki yayinda yake sauke ta saman gadon. Sai ta kara fashewa da kuka shi kuma ya saka mata dariya. “Kin cika raki, ba da gaske na ke ba, ruwa zan hada miki” Bandakin ya shiga ya hada mata ruwan zafi, ya fito yana fada mata “Kullum ki rika yin tsarki da ruwan zafi” “Wallahi ko wuta na saka ba zai daina ba, ni kaina na san zafin da na ke ji, har ya fi na jiya ma, kuma har yanzu bana iya tafiya daidai” Ta fada tana wani irin shan iska saboda kukan ya mata yawa. “Na lura ai ba zan sake ba” “Har abada?” Yayi wata mahaukaciyar dariya sannan yaja kunnenta. “Yes har a bada” Sannan ya fice daga dakin, falo ya koma ya zauna for a while sannan ya taso ya dawo dakin ya shirya cikin wasu tufafin, sai ga Ataa ta fito daga bandakin tana ta sauri. “Ka ce zaka kai ni gurin Nana ko yau?” “Ke fa baki da wyo ya za ayi Amarya da fita yau? Kuma da rana? Da ma da rana ne zan iya kai ki ki ganta sai dai kuma ba a yadda kike ba wannan abun kunya kawai zai sa na ji” “Zan yi tafiya daidai” “Ba kya iyawa ai, dole sai kin warke idan kin warke zan kai ki gida ki ga Mama da Momy” Ya fada yana fesawa jikinsa turare sannan ya juyo ya sumbace ya saka bakinsa cikin nata bayan ya cire ya shafa kumatunta. “I love you” ATAA POV. Da kallo na bi shi har ya fice sannan na zauna bakin gadon ina dan sake jikina ina hawaye, gaba daya satin haka nai shi cikin takura domin daga kafan da yai min na kwana hudu ne kawai, ranar da na cika sati daya ya kai ni da dare na ha Nana ranar ji nai kamar karna dawo gida, daker na shiga motar ina ta kuka yana jin ba dadi. Muna kama hanyar gida ya mika hannu ya rika hannuna yana ta murzawa a hankali, kamin ya kwanta da ni jikinsa. “Ashe ba za ki iya zuwa wata kasar ki barta ba? Gashe na shirya nan da kwana uku za mu dawo mu musu bankwana mu wuce” Ni dai ban ce masa komai ba sai kukan na ke a hankali, da gangan na feshe masa majigina a jikin shaddarsa na yi tunanin ko zai yi magana ne, sai dariyarsa na ji ya shafa kaina. “Kurciyarki na burge ni, dan kin yi hakan sai na ji haushi? Ko na miki fada? Ai ko ba amarya kike ba bana da irin wannan rayuwar balle kina Amarya ai ba kyan laifi ko kin kashe dan masu gida” Nan ma ban ce masa komai ba, yana rikw da hannuna yana watsa da yatsuna har muka isa gaban wani mai siyarda kilishin ya siya mana sannan muka nufi gida. Kamar yadda ya fada after three days muka koma gida dan yin bankwana da Momy da kuma Nana akan tafiyar da zamu yi Los Vegas, ya bada dama na zabi kasar da na ke son muje amman ban xaba ba saboda ban san komai akan wasu kasashen ba ni dai burina kawai na hau jirgi na san na taba hawa jirgi ko da sau daya ne a rayuwata. Rabar a gida na wuni a nan Nana take labarta min cewar ai kullum a falon Momy take wuni su yi fira saboda kadaici wani lokacin kuma idan zata kwanta Momy na turo mata Amina ko Husna su kwana tare, wani lokaci kuma ita kadai take bachinta. Na jidadin yadda Momy take kula da mahaifiyata sosai, ita kanta tana jindadin haka. Washe garin ranar muka wuce Abuja daga sokoto, Nasir ne ya hada mana komai a yadda na lura Aliyu be fada min ba, amman na lura da yawan kiransa da yake ya tambaye ni ko shi abu har tafiyar ta hadu. Ya fada min bankwana zai yi ma Mama Fulani sannan mu wuce Lagos domin daga can ne jirginmu zai tashi, be takura ni kan cewar sai yaje da ni na ga Mama Fulani ba ko kuma yi mata bakwana, ni kuma hakan ya fi min sauki da dadi, ko ba komai bana son ganinta ita da Muhseen duk kuwa da ba ni da tabbacin ko zamu tarar da shi a gidan, kwananmu daya a Abuja sannan muka wuce lagos. Daga lagos jirginmu ya tashi da ina ta jin tsoro kamar yadda nai a lokacin da zamu taso daga sokoto zuwa Abuja da kuma zuwa lagos din, domin yadda na ke tsammani da marmarin jirgi sai na tarar ya fi karfin tunani da kuma hankalina, a lokacin da zai daga kana jin motsinsa sosai idan kuma zai sauka kana jin motsin dirarsa a kasa, sai dai idan kana sama baka ma gane tafiya ake sai idan kana kusa da windows, Aliyu a gurin windows ni kuma ina gefensa ya jingina na ni da jikinsa yana ta nuna min kasashe ta cikin wata yar karamar kwanfuta dake lake bayan kujerar da ke gabanmu, da map din yake fada min yanzu muna guri kaza, wani dan biscuit ne aka kawo mana da tea shi kuma ya ce coffee yake so, bayan mun gama sha wata mai uniform ta zo ta dauke sai Aliyu ya sake maida ni jikinsa yana ba ni ragowar biscuit din da ya dauka a plate din a baki ina ci a hankali kamar wata jaririya har bachi yai gaba da ni. *Khadeeja Candy* Mun sauka a gajeye domin tafiyar jirgin ta dauke mu awanin masu yawa, na yi zaton  idan mun sauka can dare zan gani ko yamma amman sai muka samu safiya ce da alama akwai banbanci yanayi da kuma lokaci. Muna fitowa daga cikin jirgin Aliyu ya cire jacket din jikinsa ya saka min saboda yanayin sanyin garin, daman doguwar riga ce a jikina sai dan karamin mayadi daya rufe iya kaina ya sauko zuwa wuyana kadan. Kasa ce ko kuma na ce gari domin tun a jirgi Aliyu ya fada min cewar ba kasa ce gaba daya ba, gari ne dai kamar yadda kasata take nigeria da gari kala kala. Garin da zan iya kira da kasa, kasa ce yanayi mai kyau mutane kowa hada hadarsa yake babu ruwan kowa da kowa ga bin ka'idodi da dokoki ba kamar kasata nigeria ba, hannu ya daga sai ga texi ta zo ya bude min na shiga sannan aka saka kayanmu a bayan motar shi ma ya zagoyo ya shiga inda na ke, ya jani zuwa jikinsa. Ni kan idona na can jikin windows ina ta kallon tituna da kuma manyan binaye da kwaliyar garin gwanin sha'awa har muka isa wata kyakkyawar hotel mai haske da dagon bene mai kyau da daukar hankali. Na yi zaton irin kudin kasata zai bawa mutumen a lokacin daya ciro wallet dinsa, sai ga shi na ga wasu kudin ne dabam ba irin namu ba. Bayan ya gama mika masa kudin ya kama hannu muka shiga cikin hotel din shi kuma yana janye da luggage. Da yalshen nasara yai magana da su ya mika musu wani dan karamin kati da nake zaton na banki ne kamar yadda ya fada a lokacin fa yake nuna min passport din da akai min a gida Nigerian a gurin jami'in immigration da ke sokoto, da kuma na dan kasa da shi ma ya saka aka min, mayar masa da katin sukai su ka bashi wata yar takardar da makulli sannan ya juyo muka nufi wani bangare na hotel din, wani gurin ya taba sai wani dan daki ya bude mana mai kamar kumbu muka shiga ni da shi sannan ya taba wata number sai abun ya rufe ya fara tafiya da mu sama, shi kuma ya ciro wayarsa yana ta daukata hoto har muka isa abun ya bude muka fita, ni dai ina rike da hannunsa gaba daya tsoro ya gama kamani domin na lura da gurin tsif yake kamar babu kowa ga shi dakuna ne aka jera masu yawa sosai ko wane da number shi, numbobin dakunan ya rika dubuwa har muka isa gurin wanda aka ba shi key sa, budewa yai ya ya fara shiga sannan n shigo, an share dakin fes kamar wani ne a ciki komai a tsara shi gwaninb sha'awa, ac dakin ya fara kunnawa da wuta sannan ya maida kofar ya rufe ya aje kayanmu a gefen gadon. Bandaki ya shiga yai wanka da alwala ya fito sannan ni ma na shiga, bayan na gama wankan na nufo kofa abunda ban sani ba ashe Aliyu yana nan jikinn kofar labe yana jiran fitowata ina budewa sai yai cikina yana bani tsoro ai ko da gudu na koma ciki sai da yai saurin shigowa ya dauko ni ya fito da ni. Kuka na saka masa na buge masa fuska sai ya aaka min dariya wai daman ya lura da ina jin tsoro. Sai da muka lissafa sallah da ba mu yi tsakanin tasowar mu daga can zuwa nan muka rama su sannan muka dora da suba din da muka tarar a garin. Bayan mun gama ya taba telephone din gefen gadon yai magana, ba bata lokaci sai ga wani mai uniform ya kwankwasa kofar dakinmu ya miko mana abinci, Aliyu ya karbo ya kawo mana komai a cikin kwali yake sai wata yar miya ce a cikin kwankwa mai shegen ja. Ni dai ban iya cin wasu abubuwan saboda ban saba ba ban ma tana ci ba, Aliyu kan cin abunsa yake da alama ma sun fi masa dadi. Pizza na ci da shawarma sai kuma miyar da na lasa kadan sai na ji bata min dadi ba.    Bayan mun gama mu kai hauk gado mukai bachi gajiya ni da shi, yadda na ke kwana a jikin Nana haka na kwana a jikinsa, ko da muka farka lokaci ya ja sosai bayan mun yi sallah ya cire layin wayarsa ya saka wani layin dabam ya kira Momy yace ta kaiwa Nana muka gaisa sai kuma Mama Fulani ita ya kirata ta daga ya fada mata ya isa lafiya. “Miyasa ka canja liyin?” “Ai na nigeria baya yi a kira shi a wata kasar ko wace kasa da kayinta, daman na dade da siyen wannan ba yau na fara zuwa kasar” Na yi mamaki sosai jin cewar abubuwa da dama ba irin na kasata ba ne, wasu kuma dole sai an canja mutanen da yanayin ma ba daya ba.     Kwanan mu biyu a hotel din muna huga gajiya sannan muka fara fita yana nuna min wasu abubuwan da kuma wasu guraren, har da gurin shakatawa ya kai da gurin da ake hawan abubuwan wasanni kala kala, sai dai fa komai sai an biya kuma ba a jefar da abu kasa sai dai ka kasa a inda aka tanada dan zuba shara Sannan babu mata masu saka manyan Hijab ko gyale kowa ka ganinda karamin mayafi yake indan musulmi ne wasu ma musulman ne amman ba mayafa haka suke ta yawa, na ga bakar fata da dama a garin. Ba cikin Los Vegas kawai muka yi yawo ba, har ma da wasu guraren da ke kusa da ita, idan Aliyu ya nuna min wani gurin sai ya min browsing a wayarsa ya fada min gurin da irin muhimmancinsa sannan kuma yai min hoto.   Gaskiya tafiya mabudin ilmi na karu da abubuwa da dama na ga abubuwa da dama kuma na san wasu abubuwan da a da ban san su ba, mun ci abinci a restaurant dabam dabam, ido ya bude sosai da tafiyar kuma na jidadinta lallau idan dai haka honeymoon yake gobe ma a kara muje wata kasar dabam su ma muga abubuwansu. Tafiyar da mukai ba kadan ta karamin kaunar Aliyu ba, domin ya nuna min kulawa sosai da kauna, duk inda za mu je yana rike da hannu duk kuma wani abun da yasan idan n saka zai min kyau sai da ya siya min, idan kuma na ci har sai na ture, kullum sai ya kira min Nana da Momynsa mun gaisa Mama Fulani ce kawai be yaba ba ni mun gaisa ba, I love you shine furuncinsa a gareni kullum, ko numfashi nai da karfi sai ya tambaya idan lafiya nake, abun har mamaki yake ba kamar ba Aliyu ba ashe dai waje ne wannan bazaranar take a gidan kuma yafi kowa iya tarairaya da nuna kulawa, sai dai idan abun nashi ya motsa na kin magana sai ya share ni nai ta tambayarsa abu sai dai yai min murmushi ko ya ja kunne na ko hanci ya ce nai shiru idan mun koma gida zai fada min. Satin mu hudu a can sam ko mamari komawa gida bana yi domin kullum muka fita wani gurin dabam yake kai ni mai nishadi da shakatawa idan ma ta kama wani lokacin ba za mu kwana a hotel din ba sai dai mu kwana a wata. Ranar da za mu bar Los Vegas mu koma gida sai da na ji kamar nai kuka domin na fara sabawa da garin da ba nawa ba, Aliyu yana ta rarashin na yana fada min wata rana ai za mu dawo. RAHMA POV kowa yana ta hada hadar zuwa dinner da za'ayi a yau ta kanwarta Amra ita kan tana makota gidan su Lubna ta boye kanta abun duniya ya isheta, daman tun da ta ji zancen Aliyu ya tafi Honeymoon da Ataa sai ta ji gaba daya kamar bata da lafiya a jikinta yar walwalar da take sai ta daina. Kullum tana cikin damuwa da bakinciki kuka kan babu ranar da bata yinsa, tun tana ganin laifin Aliyu har ta koma dorawa Mommynta laifi a ganinta da bata yi mahaifiyarsa wannan cin mutuncin ba da yanzu be kara auren ba, kuma da yanzu tana can dakinta. Wannan tunanin shi ya hanata sakewa kuma ya hanata sukuni balle har tai murna ko walwala a cikin yan'uwanta da yan biki. “Rahma kina ta sakawa kanki damuwa dubi ki ga yadda kika koma, kowa yana can yanashirin zuwa dinner ke kina nan kin ware kanki dabam kina ta saka damuwa a ranki saboda da namiji” Rahma ta kalli Lubna wacce ta dafata tana wannan maganar. “Lubna idan ban yi kuka na yi damuwa ba dariya kike son nai na yi murna Aliyu yayi aure? Ina son miji taya zan jure ganinsa da wata?” Ta fada cikin kuka. “Indai kina son mijinki Rahma dole ki yi hakuri ki koma dakinki, ba dole sai kin tsaya ya zo bikonki tunda dai kin san laifi na ki ne, kin dawo gida kin zauna kina fushi kin bar shi can shi kadai kuma mahaifiyarki ta hana shi ke lokacin da mahaifiyarshi ta zo bikonki kuma ki yi tsammani ba zai yi fushi ba? Haba dai ai Wallahi dole ma ne mahaifiyarsa ta saka ya kara aure, ni dai inda nake ganin rashin kyautawarsa na kin dawowa yai bikonki gaskiya be kyauta ba, sai dai idan aka aunanda tafiyarki Dubai ba ki fada masa ba sai a ga kamar hakan da yai ya dace” “Ki daina tuna min abunda ya riga ya faru, ki ba ni shawarar abunda zan yi” “Shawara kawai ki koma dakinki, ko da iyayenki sun nuna miki ba haka ba ki ce ke dai kina son mijinki kuma kina son ki koma dakinki, amman zamanki a nan ai matsala ce kawai domin za ki jawa kanki wata matsalar ne wata kila ma ki janyo ciwon ya dawo gashi har yanzu ba a samu kodar ba” Shiru tai na wani lokaci sannan ya hade ya wu ta ce. “Zan koma, idan an daura auren Amra gobe hankalin Daddyn ya kwanta zan masa magana, na san yanzu hankalinsa ba kwance yake ba saboda zuwan Mai Martaba Sarkin Agadaz” Lubna ta wara ido, domin ita ma tana jin labarinsa saboda tashen kudi da siyen kamfaninika da yake. “Laa ya zo? Ashe dai da gaske zai zo” Rahma ta share hawayen. “Eh ai bashi da girman kai, daman Daddy ya ce zai zo domin shi ya bawa walincin aurar da Amra, kuma daman yana bukatar zuwa da kansa yi ma Daddy jajayen rasa babban shopping mall dinsa da kuma duba wasu abubuwam tun yau ya zo ance yana Hotel yana hutawa sai gobe zai je daurin aure idan an daura zai wuce Abuja ya duba wasu abubuwan sannan yaje jigawa da Lagos sai kuma ya wuce, tun da yamma ma Mommy ta shirya masa abubuwa taje ita da Daddyn suka kai masa, hankalin Daddyn yanzu yana can gurinsa amman na san da zarar an daura auren ya wuce Abuja indai ba tare da Daddy za su tafi ba zan samu ganinsa hankali kwance idan ma da shi yaje ai dole Daddyn zai dawo sai na fada musu cewar ni ina son komawa dakina” “Ba dole sai Daddy kai tsaye ba, idan dai hankali ya kwanta sarkin ya tafi an gama bikin sai ki samu Mommynki a daki ki fada mata ita zata fadawa Daddynku ai” “Amman kara na same shi ni da kaina dan ya tabbatar da gaske na ke, saboda Mommy zata iya kin fada masa, tunda bata son komawar tawa” “Ke dai ki gwada idan ka bata fada masa ba ai sai ki same shi da kanki ke ki fada masa daga baya” Ta gyada kai. “Zan yi hakan In-Sha-Allah na gode sosai Lubna” “Karki damu,  kuma idan kin koma ki nuna mata ruwa ba sa'an kwado ba ne, kin dai san ba lafiya ce ta ishe ki ba Wallahi ko bi tai kusa da ke ki fadi ki ce ta tureki dole ya daukar mata mataki ki tai mata bandar kasa” “Ai ba sai kin fada min wannan ba, ke dai na koma gidan kawai tana yadda ake kula da mijin tana wata kazamarta komai bata iya ba, sai ya san banbancina da ita ai dole” “Ina son ki kawata, ai kema na san baki da dama kina babbar mace karamar yarinya ta ce zata zubar miki da aji? No-no yanzu dai tashi muje gida ki shirya muje dinner ki cire komai a ranki yanzu mun samu mafita” Murmushin jindadi Rahma tai ta mike tsaye tana dora mayafinta a wuyanta, tare da kallon kawarta. “Bari na je na shirya ke ma ki shirya sai na zo mu tafi domin ni motata tana can gurin hadahadar biki ana yi da ita” “Ba matsala bari nima na shirya” Daga haka itama ta mike tsaye ya rako Rahma har gurin gate din gidansu suna ta kara tattaunawa kan lamarin kamin Rahma ta wuce gidansu domin shiryawa ita ma Lubna ta koma gida. ATAA POV. Kusan karfe ukun dare muka baro can kayan da muka tafi da su da zamu dawo sai mu dawo da jaka biyu, domin a lokacin da zamu je tufafina da na shi a jaka daya ya hade su, tsarabar da mukai a can kuma ta zama a dayar jaka ya zama mun dawo da jaka biyu a amaimakon daya da muka je da ita. A lagos muka sauka kamar yadda muka tashi a can, na yi zaton ko Aliyu zai bari sai idan mun huta a lagos din sannan mu wuce Abuja ashe duka rana daya ne banbancin awa biyu ne kawai na jiran da mukai, tun da muka sauka a Abuja na soma jin kamar ba ni da lafiya kaina sai ciwo yake jikina yai zafi wata kila saboda canjin yanayi ne domin yanayin can ya fi na nan dadi sa sanyi, wata kila kuma saboda gajiya ne domin ban saba irin wannan tafiyar ba. Yamma ta yi a nan domin karfe uku ne har yan mintuna a nan Abuja. Muna sauka airport Aliyu ya kira Nasir ya fada masa, ba bata lokaci sai gashi ya zo da motarsa ya dauke mu. Dan kwantawa nai a kujerar baya wai ko zan samu walwala da sakewa kamin mu isa gida, amman sai karuwa na ke jin abun na yi sanyin ac motar ya sa ina jinsa ba dadi kamar nai amai, yawuna ma daker na ke iya hadewa. Lokaci lokaci Aliyu ya ke dan waigo baya ya kalleni sai na masa murmushi ina kokarin nuna kamar bana jin komai amman hakan be hana shi ya gane ba. “Baby za muje gurin Mama idan mun huta a can sai mu wuce gidanmu kin ji?” Na ji ba dadi domin ba son ganin Mama Fulani na ke ba domin bana sakewa da ita kuma na san ba so na take ba har yanzu. “Amman ba za mu fara zuwa gida mu huta ba, idan mun huta sai muje mu gaishe ta?” “No na riga na saba indai na yi tafiya mai nauyi irin wannan idan zan dawo gidanta na ke sauka zata shirya min abubuwa masu kyau, idan kuma a sokoto ne gurin Momy na ke sauka, amman ba za mu dade ba tun da ba ki da lafiya” Babu yadda na iya tunda ya fada min haka akidarsa take amman har ga Allah bana son ganin Mama Fulani gabana har faduwa yake. “Ba ta da lafiya ne?” “Eh nima yanzu na lura” “Ayyah Maybe gajiya ce” Nasir ya tambaya yana juyawo ya kalleni. Sai Aliyu yai masa wani kallo. “Ya zaka leko ka kallar min mata? Ni fa bana son haka” “Kallon ta kawai nai fa” Nasir ya fada yana dariya. “Ato ko kallo ai ba zan jidadi ba, yanzu nan sai shedan ya raya maka wani abu, kasan mata masu kyau hadari ne” “Kai Allah ya kiyaye wannan abun” “Ato kodai cewa kai tana da kyau a zuciyarka ai na ji haushi” Ban da dariya babu abunda Nasir yake har nima nai murmushin. Kamar yadda ya fada a gidansu Mama Fulani Nasir ya sauke mu, sai dai na lura kamar suna da baki domin na ga manyan motoci na alfarma da bansan da su ba a gidan har biyu, wata kila kuma na Muhseen ne ko mahaifinsa wadanda ban san da su ba. kin fitowa nai daga motar har sai da Aliyu ya fita ya zo ya bude min sannan na fito cikin yanayin da ke nuna bana jindadin zuwa gidan ba kuma dan fargabar komai ba sai na abunda zai iya biyowa baya. “Ki kwantar da hankali ina tare da ke ai ko?” Na gyada kai, ina tuna zama na a gidan a matsayin mai aiki yau kuma na shigo a matsayin matar Aliyu daraja ta dagu, sai da ya rufe motar sannan ya rika hannuna babu ko kunya muka shiga ciki. Da sallama ya shiga yana janye da hannuna da nake kokarin kwacewa ya ki ya sake. Ina jin yadda Mama Fulani ta amsa masa ita da su Maryam cikin far'ar da jindadin ganinsa. “Maraba maraba da dan tafiya ka dawo lafiya?” Ta fada ba tare da ta kalleni ba, Aliyu kawai take kallo. Tana sanyi da wata tsaddadiyar shadda ga yan kunnen gol da sarkarsu ta zuba a wuyanta Maryam da Rukaiya sun ci kwaliya kamar masu zuwa biki. A kujerar dake fuskantar tata ya zauna yana murmushi har lokacin yana rike da hannuna sai ya tangwarani ni ma na zauna. “Mun dawo lafiya Mama fatar mun same ki lafiya?” “Kai kadai na tambaya ai kai da wani kai tafiyar ne?” Ya yi shiru be ce komai ba ni kuma nai kasa da kaina ina mika mata gaisuwa. “Barka da yamma Mama Fulani” Sai tai kamar ba ta san da zamana a gurin ba balle har ta amsa min sai magana take ma Maryam wai ta dauko ma Aliyu fruits din data yanka masa. Idona ne ya cika da kwalla ina kallon Aliyu sai ya girgiza min kai alamar kar nai kuka, a dole na maida kukan ciki. “Biki ake ne Mama na ga kun yi kwalliya” Ya fada bayan Mama Fulani ta miko masa ruwa mai sanyi. “Eh baka ga motoci a waje ba? Mai gidan Abbahku ne ya zo, ya so ya sauka hotel Abbah ku ya dage ya roke a akan ya sauka gidanshi idan ya huta sai su shiga ya duba kamfanin har da surukin ka aka zo ai baban Rahma” Aliyu ya sha ruwan sannan ya miko min har zan karba sai ta daka min tsawa. “Karki kuskura ki taba min kofi, wai ba na fada maka karka kuskura ka kawo ta a gidana ba? Ban gargade ka ba?” Karbar kofin Aliyu yai yaje. “Mama idan kina takura mata ba dadi zan ji ba yanzu fa ita matata ce, Wallahi ko lafiya bata da” “Ni ma saka mata ciwon kenan? Ka dauki yarinya kanta na cikin keji ka ta ka kaita har Los Vegas, ai Wallahi ka gama da turawan can ka gama ci musu mutunci” Aliyu be sake cewa komai ba sai kallona yake domin tuni hawaye sun fara wanke min fuska, ina da dannar kukana domin ina daf da fashewa da kukan. Maryam da Rukaiya dai ba su ce komai ba na san hakan baya rasa nasaba da ganin Aliyu a gurin. “Ai Wallahi ba dan zuwa Sarki Agadez a yau ba, ina cikin farin ciki da Wallahi abunda zan mata ba zata sake marmarin gani na ba balle har ta dawo gidan nan” “Sarkin Agadaz?” Na tambaya da sauri ina dago kaina na kalli Mama Fulani jin sunan sarkin yasa na manta da kukana a take. “Sarkin ubanki, idan na sake magana kika saka min baki sai na saka Rukaiya ko Maryam sun fitar miki da jini a baki” Ta fada tana aiko min zagi da hannunta. Ban damu ba ya koma gurin Aliyu. “Aliyu sarkin Agadaz yana nan cikin gidan kenan? Ko kuma garin nan yanzo?” “Yana nan cikin gidan yana part din Abbah” Ya fada yana kai hannunsa ya share min hawayena. “To sarkin soyayyah ai ban san kana son ta ba sai ka dauke wannan kazamar ka hade, sai na san kai din baban soyayya ne ko kuma kana son ta, wai ko kunya baka ji Aliyu kalle ka ace ka kare a wannan abun, ai Wallahi Rahma bata cire haushi ba” Shine abunda Mama Fulani ta fada ni kuma na mike tsaye jikina na rawa na ce. “Aliyu ina son na ganshi ina son na ganshi Aliyu dan Allah” “Ai dole ki so ganinsa kan ki kafa tarihin ganin mai arziki a rayuwarki yar matsiyata” Ban kula maganar Mama Fulani ba na soma fashewa Aliyu da kuka. “Ina son na ganshi Aliyu dan Allah” Mikewa yai tsaye yana kallona ganin da gaske kuka na ke. “Lafiya minene?” “Ina son ganinsa yanzu yi sauri ka kai ni dan Allah” “Karka kuskura shiga da ita ita Mai Martaba baya son damuwa, ganin yarinyar nan ma zai iya sa masa tashin zuciya” Tsayawa yai kallona sai na bar shi a gurin ya nufi kofa da sauri ina kuka duk ban tana shiga bangaren Abbah ba yau zan je na shiga, ina fitowa na ji ya riko ni ya juyo da ni. “Baby lafiya kike?” “So na ke na gani idan shi ne da gaske idan ba shi ne zan fada maka” “Okay” Ya ja hannuna sai ya nufi wata hanya da ni mai kamar corridor duk zamana gidan ban tana binta ba sai yau. Wani gurin muka kullo sai ga wani dan karamin guri mai kamar mai yar rufa da wata babbar kofa a ciki, ta kofar ya murda ya shiga da ni ciki sai da mukai yar yafiya kadan sannan ya tsaya da ni gurin windows falon a nan ma wani a tsaye yana kokarin tare window. “Kalla ki gani shine mi yai?” Kallonasa nai sai na hango zaune saman kujera tsohone sosai amman ba irin tsufan nan na marasa karfi ba, irin tsufan nan da jindadi da wadata wanda tsufan sai ya tsufa sosai a jikinka yake bayyana kansa, farin waganbari ne a jikinsa ya hade fuskarsa da rawani wasu matasan samari na zaune kusa da shi a kasa, mahaifin Rahma da Abbah na zaune kasa suna masa fira a hankali da alama wani abun Abbah yake nuna masa Daddyn Rahma na kara masa bayani. Tsufansa be hana ni ganin fuskar Nana a fuskarsa ba, kuka ne ya zo a take na kalli Aliyu ina fadin. “Shine Aliyu shine Mahaifin Nana” Ina fadar hakan nai saurin kufar inda na ke hango dogarai masu wasu kalar tufafi da ba kalar na dogaran nan ba da zimmar shiga sai suka tare. Ashe kofar ma ta cikin gida su suke tsaronta har da wasu masu shigar gida da nake kyautata zaton yan sanda ne amman ba su saka uniform ba. Dawowa nai da gudu gurin windows din na tura bakina da inda muryata zata shiga cikin falon. “Mai martaba ina son na ganka sun hana ni” Na fada cikin daga murya da yaren buzanci, sai mutane da ke tarun kofar da tagar suka yo kaina da sauri za su rike ni, Aliyu yai sauri jana ya maida bayansa. “Kar wanda ya taba min mata cikinki” Ya fada yana nuna su da yatsa. “Mai Martaba” Na sake kiransa sunansa da yaren buzanci ina kuka. Sai ga Abbah ya fito tare da Daddyn Rahma. “Miye haka?” Abbah ya fada yana tambaya da hannu cikin bacin rai, har Aliyu ya bude baki yai magana sai ga daya daga cikin samarin da ke tare da sarkin ya fito da hanzari yana kallona. “Wacece ke?” “Ni jininsa ce ni yar Asma'u ce ni yar Nana Asma'u ce dan Allah ku bar ni na ganshi?” “Wace Asma'u?” “Gimbiya Nana Asma'u yarsa dan Allah ku bar ni na ganshi” Duk da yaren buzanci muke magana da saurayin, kamin mamaki ya kamashi sai yai min wani kallo daga kasa zuwa sama sannan ya juya ya koma ciki da sauri. Be dade ba ya dawo ya ce a shigo da ni, da sauri na shiga gaba wajen shiga cikin falon. Sai dai ina shiga sai dogaransa suka hana ni isa kusa da shi. “Wallahi ni jininka ce Mai Martaba ni yar Asma'u ce ba cutar da kai zan ba” Na fada cikin yaren buzanci ina kuka, kallo yake daga can inda yake zaune, har na wani lokaci sai ya daga musu hannu sai suka bani guri na nufi inda yake da sauri, ina isa na fadi kasa na rike kafafunsa na fashe da wani irin kuka. *Z A K I -it's not free, pay 300 to 0314795884 Abubakar Gt bank, then send the evidence via 08036126660* *AG cera ya zo domin ya temaki garkuwan jiki da kuma lafiyar jiki. Sinadari ne wanda ze magance matsaloli da dama wadanda suke hana garkuwan jiki aiki yadda ya kamata ko kuma yake rusa garkuwan jikin ita kanta.* *Cututtukan zamani daban daban sun sa mutane gaba kuma magance su yana da wahala; irin ciwon Sugar, hawan jini, ciwon sanyin kashi, ciwon gabobi da sauran su. Haka ma cutukka irin wadanda suka shafi fatar jikin wadanda sun hada da kyasfi, pimples, takurewar fata, rakainuwar fata da kuma haske da kyallin fata duka ana shan AG cera kuma yana temakawa wajen magance illolin nan. Mutane masu fama da rashin karfin jiki wajen kwanciya da iyali da kuma mata masu fama da yawan ciwon mara lokacin al'ada ta karshen wata suma baa bar su a baya ba. A takaice dai AG Cera yana temakawa wajen magance cuttukka daban daban wadan ke damun mutum. Domin karin bayani ku tuntuni mu a wannan number +60167474649 ko kuma ku ziyarci shafin mu http://agnutritioninternational.com.* Wani irin kuka na ke bai ban tausayi da taba zuciya ni kaina ina jin wani yanayi da ban taba jin irinsa a sai yau, taya zan iya bayyana ganin farinciki? Farincikin mahaifiyata? Kakana? Kai tsaye kuma a saukake ban taba kawowa raina haduwa da shi a nan kusa ba. Ban taba tsammani abun zai zo da sauki kamar haka ba. Ji nai an shafa kaina sai na dago da saurin domin tantace mai taba nin shi din ne ko wani? Shi ma kwalla ce a idonsa irin da tsufaffin da basa son bayyana kukansu. Daga cikin wanda yake tare da su ne suka zo za su rikani su raba ni da kafafuwansa da na rike sai an kara rike su da sauri na fashe da kuka, a take ya daga musu hannu Alamar su kyale ni. Wani irin kuka nake kamar dacan an halitto kukana dan zuwan wannan ranar ne kawai, tun ina a hankali har muryata ta fara shakewa, sai Aliyu ya matsa kusa da ni ya dafa yana kokarin raba ni da jikinsa. “Ayusher ya isa haka” Kai na girgiza masa na sake rike kafarsa, dadi na ke ji yau na ga wani daga dangina, yau na ga mutumen da Nana take ba ni labarinsa, ban tana gani wani dan'uwa daga jinin Nana ko jinin Mahaifina ba, sai yau taya ba zan yi kukan dadi da farinciki da tausayi da takaici a lokaci daya ba? Hannu ya daga wa Aliyu kamar yadda yai ma sauran, a dole Aliyu ya kyale ni yana ta damuwa da kukan da na ke, ni kuwa na samu damar yin kukana iya son raina har sai da na ji an samu natsuwa sannan nai shiru dan kaina amman ban sake kafar ta shi ba. Sai a lokacin na lura da hankalin kowa yana kaina, cikin har da Mama Fulani da Maryam da Rukaiya da Ammy da yayanta da ban san lokacin da suka shigo ba. “Waya fada miki cewar Mai Martaba shine kakanki? Taya za mu yarda da ke?” Dayan ya tambaya da yaren buzanci. “Ita ta fada min, kuma na ga kamaninta a fuskarsa, idan kuma kana musu ne zan iya kai ku har inda Nana take” “Asma'u.....ta....na...ra.... ye?” Wannan karon Mai Martaba ne da kansa ya tambaya maganar tana fitowa da dai daya daga bakinsa cike da kasaita da izza irin ta manyan sarakuna. “Tana raye amman bakincikin rashinka da duka danginta ya dade da kasheta, kullum mafarkina ni da ita a ina zamu ganka, ta wace hanya zan sadu da kai? Mai Martaba ba ni da kowa sai Nana aka Nana kuma vata da kowa sai kai, ban sanka ba ban taba ganinka a ido ba amman ta kwadaita min kaunarka da son ka da kuma son rayuwa da kai, kullum kukana a kanka mafarkina ni da Nana na ka ne” Lumshe ido yai ya hade ya sauke ajiyar zuciya a hankali. “Ki daina magana haka Mai Martaba baya son yawan magana, kuma ya kai matsayin da ba komai ake fada masa kai tsaye ba” Daya daga cikin samarin ya fada. Sai ya bude ido ya daga masa hannu. “Barta ta fadi iya abunda zai mata dadi, ita ma jika ce kamar kai, ita din jinin Asma'u ce Asma'u kuma jini na ce, jinina kuma na duka iyalaina ne” Duka da yaren buzanci mukai wannan maganar daga Mai Martaba har ni har jikansa na sa. Wani irin dadi ne ya lullube ni jin yadda ya kira ni jikarsa jininsa kai tsaye ba tare da tantama ba, ba kuma tare da kyama ba. Murmushi nai na sake rumgume kafafuwana ina jin wani irin sanyi da Rahama irin ta kaka da jikasa. A take na ji amai na cika min baki da sauri nai baya ina kokarin mikewa kar ma sa shi jikin nai kofa da sauri sai dai kamin na kai tuni aman ya cika min baki ni kuma na bashi hanyar fitowa. “Subhanallahi” Ammy ta fada tana nufo inda nake kamin ta kawo tuni Aliyu ya zo ya rika ni, shi ya fito rike da ni harabar wajen na fara sheka amai kamar zan amayarda duka hanjina domin har ta hanci zubo min yake ban taba amai mai wahala irin wannan ba. Ina gamawa Aliyu ya zaunar da ni Batula ta dauko ruwan gora ta miko masa ya wanke min fuskata ya zuba min a hannunsa ya dura min a baki na kuskure ya zubar. “Sannu” Ya fada cike da tausayawa, sai na gyada masa kai ina jin wani irin jiri na dibana kaina kuma yana ciwo sosai har bana son daga idona. “Bari na janyo mota sai muje asibiti” “Aa bana so dan Allah” Na fada da saurin domin har ga Allah bana son zuwa asibitin, daman can ni asbiti ba burgeni take ba, kuma ina ganin idan na bar gidan Sarkin Agadaz zai iya tafiyarsa ban sake magana da shi ba. “Amman jikinki ya yi zafi sosai kuma.... ” “Aliyu idan bata son asibitin ka barta tasha magani sai ta kwanta idan idan ta farka abun be sauka ba, sai a tafi asibitin” Ammy ta fada ganin zan saka kuka saboda kawai ance aje asibitin. “Aa ni bana jin bachin ma” Na fada idona na cika da kwalla. “Aliyu mu koma ciki ina son magana da shi” “Ki barshi ya huta idan ya huta zai ce a kira ki ai” Aliyu be gama rufe ba ki ba, sai ga daya daga cikin jikansa ya fito yana fada min Mai Martaba na son ganina. Da sauri na mike tsaye sai Aliyu ya rikani domin bana iya tafiya da sauri jikina kuma ba karfi ga jiri na dibata, daf da zamu shige bangaren Abbah muka ji tsayarwar mota, sai na waigo na hango Muhseen ya fito daga motar da waya a kunnensa, ni kuma na juyar da kaina muka shiga cikin falon, wannan karon babu kowa a ciki sai shi kadai da jikokin nasa. Daga bakin kofar Aliyu ya tsaya ya bar ni ni na wuce can ciki. Kasa na zube kusa da shi na zauna yana ta kallona a hankali ni kuma nai fuskar tausayi ya langwabar da kaina ina kallon kasa. “Ina Asma'u take?” “Tana sakkwato” Na amsa mishi da sauri cike da kaguwar jin abunda zai sake fada. “Ta fada miki dalilin rashin danginta a kusa da ita?” “Ta fada min kuskuren da ta aikata, kuma ta yi nadama sai dai ta ce ba zata koma gareka ba har abada saboda abunda ta aikata maka, ta ce ta saka masarautarsu a kunya, da maka butulci ba zata sake dawowa gareka ba saboda ba zaka taba gafarta mata ba, ta yi kukan rashinka ta shiga matsalolin rayuwa ta rasa muhallin zama da abun sakawa a baki saboda butulcin da tai maka, a cikin abubuwan da ta rasa mai martaba har da lafiyarta, kuma ta alakanta hakan da butulce ma iyayenta da tai, a kullum tana fada min rayuwarta ba mai tsawo ba ce ta min umarnin na nemi danginta bayan rayuwarta kuma na roka mata gafararka da na su, ta haife mu ni da kanena shi ma har ya rasu gurin bara be san ka ba, tana bakincikin gina wata rayuwar ba tare da kai ba, da ni da ita duka rayuwarmu a titi ne sai mun yi bara muke ci, gidan kuma za mu kwanta sai dai mu raba a gidan wasu mu kwana” Tun da na soma maganar yake ta jinke hannusa da sandar da ke hannun nasa, da alama maganganun da na ke masa sun taba masa zuciya ko kuma basa masa dadi. “Ina Umar?” “Ya rasu, Nana ce kawai ta rage sai ni” Na fada cikin kuka, sai ya mika hannunsa da sauri jikan nasa ya risino yana sauraren maganar da ke fitowa daga bakinsa kadan-kadan. “Ta fada muku inda Asma'u take ku je ku taho da ita” A take ya karaso inda na ke yana tambayata da yarenmu. “Ina Asma'u take?” A take na fada masa, sai ya fice daga falon. “Tashi kije ciki zan je masaukina” Mai Martaba ya fada min, sai na mike tsaye ina jin kamar kar na tafi na fito daga dakin, sai na samu Aliyu a tsaye yana jirana. “Kin yi magana da shi?” Ba gyada masa kai. “Eh yace zai je masaukinsa” “To muje ciki ki huta” “Mama Fulani ba zata bar ni na shiga dakinta ba, na kai ni gurin Ammy” Na fada ba dan ina da tabbacin Mama Fulani zata hana ni shigar ba, sai dan na fi son Ammy da ita kuma zan fi sakewa a can. Be min musu ba ya gyada min kai sannan muka sauko tare muka nufi bangaren Ammy. Muna shiga falon Zee da Humaira suka fara min sannu na amsa musu har da Inteesar da ke ta daukin ganina. “Ataa mun yi missing dinki sosai” Ban ce mata komai ba bayan murmushin karfin hali da nai mata, sai Aliyu ya kalli Zee ya ce. “Zainab kwantawa za tai a dakinki kar motsi ko wani hayani ya tashe ta dan Allah” “Okay ya Aliyu” Ta hannu yai min alama da na wuce sai ya bi bayana, har muka shiga dakin saman gado na haye abuna sai ya dauko filo ya dora min a gurin kafafuwana sukai sama. “Sannu” Ya fada yana taba kaina. “Na gode” Na fada ina kallonsa da fafaren idanuwana. “Amman Babyna da gaske mahaifin Mama ne? Hakan na nufin kakanki ne kenan?” Na gyada kai. Mamaki ne karara a fuskarsa kamar zai sake tambayata sai kuma yai shiru ya zauna gefen gadon kusa da ni. “Akwai abubuwan mamaki a wannan maganar ta ki, amman lafiyarki ta fi muhimmancin a gareni, runtse idonki ki ja numfashi da karfi ki sauke a hankali ki saki tunaninki za ki samu bachi yanzu nan” Yadda ya fada min haka nai a take kuwa bachi yai gaba da ni daman bachin ne a ido na. ALIYU POV. yana ganin ta yi bachi ya taso ta baro mata dakin tare da jan kofar a hankali ya kulle, part din Mama Fulani ya dawo a inda ya same ta cikin falon ta kasa zaune ta kasa tsaye, tana ganinsa sai tai saurin zaunawa tana kallo kofa ko zata ga Ataa ta shigo, da ta bata shigo ba sai tai kasa da murya kar wani ya ji kamar ba daga ita sai shi ne a falon ba. “Aliyu na ce wai ita wannan Ataa daga ina take? Na ga ta rike kafafuwan sarkin Agadaz tana kuka suna buranci, na ce ko ta masa aiki ne a can kamin su dawo nan da zama?” “Aa ta fada min cewar kakanta ne shine ya haifi mahaifiyarta” Mama Fulani ta daki kirji tana zaro ido. “Kakanta? Kaka kaka kaka fa? Kakanta fa? Ai idan mai fada ba shi da hankali mai ji yana da shi” “Amman Mama Ayusher ba zata min karya ba” “To ni kuma sai na yarda tunda gani fulanin mahaukata ko? Yarinya yar titi yar bara rana daya zata ce ita jikar wannan mutumen ce sai kuma sai na yarda ko? Jikarsa zata zo ta mana aiki? Har tai bara? Na yarda dai ta masa aiki a can Masautarsu, oh na ma tuna ina jin babarta baiwa ce su bayin Masautar ne” “Wata kila kuma da gaske take yi Mama, tun da har kika ga ya kyaleta kuma ya aiko a kira ai kin san yana da alaka da ita, kuma bana zaton Ayusher zata karya, wata kila wata kaddararce ta saka suka tsinci kansu a cikin wannan halin rayuwar” “Uhm Aliyu baka da wayo wallahi taya za 'ayi tana jikar sarki ta zauna a nan ko tai bara? Ai da kowa sai ya jiya, kuma ko dukansu yake kullum sai sun zauna a inda yake, yanzu ma ina ga aiki suka masa ko kuma bayin masarautar ne shiyasa lokacin da ta ji sunansa hankalinta ya tashi ita dai ta ganshi” “Ko ma minene dai za a warware shi very” Mama Fulani taja wani dogon numfashi ta sauke tana girgiza kai. “Kai ba haka ba ne, sam ina... Ba za zai yiyu ba” Ta kasa yarda da abunda Aliyu ya fada mata taya ma zata yarda wai wata Ataa jinin wannan sarkin ce. Sai dai wani abun amman bata yarda ba, Aliyu ya mike tsaye ya nufi kitchen kenan sai ga Abbah ya shigo yana gyara babbar rigarsa. “Hajiya Fulani za mu je sokoto yanzu nan” “Sokoto kuma? Gurin me?” “Mai Martaba ya ce aje a dauko masa mahaifiyar Ataa, da jirginsa da ya zo da shi za a aje kin ga ko tunda gida ne ai da ni za a aje” “Mahaifiyar Ataaa?” Ta fada tana dukan kirjinta har da wani kashe ido take. “Mahaifiyar Ataa fa kace Alhaji?” “Eh ita fa kin san tana gidan Momy” “To ina jin wata babbar sata suka masa lokacin da sukai zama gidansa, ina lokacin da suke bayinsa sun masa wata katuwar sata ko kuma hasara, shiyasa Ataa take kuka tana rike kafafuwansa so take ya yafe musu” Mama Fulani ta fada tana gyada kai. “Amman abunda shi jikan nasa da suka zo tare yake fada mana wai Mahaifiyar Ataa ita ce yar Mai martaba” “Aehhhh ya fa ka ce?” Ta tambaya da karfi tana zaro ido. “Eh Wallahi ni kan na ce ai sun warke” “Aa ba wani zancen warkewa ina jin dai yana nufin yarsa ta gari tun da shi sarki ai baban kowa ne, balle mutane masu nijar kasan yadda suke da junansu” “Ko ma minene dai ai shi Mai Martaba zai fada da kansa, yanzu haka har ya wuce gidansa da ke nan yana jiranta, da ko be yi niyar zuwa gidan ba hotel ma zai sauka ni ne dai na dage ya sauka a nan ashe kin ga abo ne,sai muj dawo” Abbah na fadar hakan ya juya ya fice da sauri. Mama Fulani ta rumfume hannayenta a kirji sai girgiza kai take. “Aa ina ai ba zai yayu ba sam” Duk abunda suke Aliyu na jikin kofar kitchen din rike da ruwa yana sha, shi kanshi mamakin abun yake ya san Ataa ba zata masa karya ba, kuma yadda ya ga Sarki ya nuna mata kukarwarsa ya san dole akwai alaka mai karfi a tsakaninsu, gashi kuma yanzu har ya ce aje a taho masa da ita, sai dai be san taya ta bar gidansu ba mi ya faru har suka tsinci kansu a cikin wannan rayuwar. Gaba daya Mama Fulani kasa sukuni tai zuciyara na son yarda kuma tana jin yarda idan ta duba wasu abubuwan da suka faru, abun na ta cinta kamin su Abbah su kai har ta kira Momy ta labarta mata abunda ya faru, ita ma kanta Momy ba karamin mamaki tai ba jin abun kai tsaye kamar daga sama a take mamaki ya cika ta. Bayan ta gama da Momy kuma ta koma tana tatauna maganar da su Maryam da Rukaiya Maryam ce tai saurin yarda yayinda Rukaiyah kuma ta tsaya kwankwato. “Idan kuma da gaske ne fa Mama? Kina ganin da ba jikarsa ba ce zai kyaleta ta rike masa kafa kuma tai ta masa kuka haka har kuma ya ce a aje a dauko masa mamanta? Gaskiya ina ganin gaskiya ne” “Ai sarakuna suna da wannan karancin, kin san ai wasu suka rika kafafuwan manyan mutane saboda neman gafara ko kuma tubarraki, amman ba gaskiya ba ne” “Gaskiya ni ma ban yarda ba, ai ko da mai unguwa kake da alaka sai an ji balle kuma mutum irin wannan, ai ko kama ma ba su yi ba” “Eh ba su da kama fa, yauwa Rukaiya ashe kin gane, ina jin dai ba yin sa ne ada can da” Haka sukai ta tattauna maganar a tsakaninsu daga Mama Fulani har Maryam da Rukaiya da kuma Baby wacce bata ce komai ba mamaki suke suna Ala ala abun ya zama ba gaskiya ba. Aliyu kan yana ta an ya tare a bangaren Ammy yana cin abinci shi da matarsa wacce bata dade da farkawa ba. Ya jidadin yadda ta farka zazzabi ya sauka duk kuwa da kasancewar bata sha magani ba a lokacin da zata kwanta. ATAA POV. Na farka da tunanin Nana a can cikin mafarkina kuma abunda ya faru dazun nai mafarki, babu komai a raina sai son ganin irin yadda Nana za tai idan ta ji cewar na hadu da Babanta ko kuma Mahaifiya ce aje a taho da ita. Ina ma ace ina can na na ga irin kukan farinciki da za tai da kuma irin rudewar da za tai. Ina cikin wannan tunanin Batula ta shigo sai nai saurarin share hawayena. “Ya jikin” “Na ji sauki” Na amsa har lokacin hawaye na sauko min. “Ya Aliyu ya ce na tashe ki ki yi sallah magariba ki ci abinci idan zazzabi be sauka ba za ku je asibiti” Sai da tai maganar na tuna da cewar da yamma na kwanta, ashe har magariba ta yi ban sani ba, lallai na dan yi kwanan da nauyi. “Ki fada masa na ji sauki” Na amsa ta ina gashi na nufi bandaki da yin alwala so na ke nai sallah sannan na saka Aliyu ya kira min Momy ta bawa Nana mu yi waya, na fara yi mata wannan albishir din kamin kowa ya mata domin an san ba za a je daukarta a yau ba idan ma anje yau sai gobe za su iya ko kuma cikin dare, waya sani ma ko za su tsaya tsaya jiran jirgi kuma ace babu jirgin sannan na da wasu hours. A gagauce nai alwalar ina fitowa sai an samu Aliyu zaune a kasa Inteesar na jera mana abinci shi kuma idonsa na kaina kamar zai cinye ni. “Ya jikinki” “Na ji sauki, Aliyu idan mun yi sallah za ka kira nin Nana?” “Yes amman sai mun fara cin abinci tukuna” hijab din Zee na saka nai sallah har yai na gama na yi addu'a idon Aliyu na kaina, kamin na juyo har ya bude fular tuwon ya soma zubawa a a plate, ina juyowa ya saka spoon ya fara diban abincin ya bani, kadan kadan na ke ci saboda warin miyar nake ji daker ma na ke iya hadewa a take warin manjan ya daki hancina sai na ji kamar zan yi ama da sauri na rufe bakina na nufi bandaki, shi kuma ya taso ya biyoni ina sheka aman yana shafa bayana yana min sannu cike da tausayawa. *Z A K I -it's not free, pay 300 to 0314795884 Abubakar Gt bank, then send the evidence via 08036126660* *AG cera ya zo domin ya temaki garkuwan jiki da kuma lafiyar jiki. Sinadari ne wanda ze magance matsaloli da dama wadanda suke hana garkuwan jiki aiki yadda ya kamata ko kuma yake rusa garkuwan jikin ita kanta.* *Cututtukan zamani daban daban sun sa mutane gaba kuma magance su yana da wahala; irin ciwon Sugar, hawan jini, ciwon sanyin kashi, ciwon gabobi da sauran su. Haka ma cutukka irin wadanda suka shafi fatar jikin wadanda sun hada da kyasfi, pimples, takurewar fata, rakainuwar fata da kuma haske da kyallin fata duka ana shan AG cera kuma yana temakawa wajen magance illolin nan. Mutane masu fama da rashin karfin jiki wajen kwanciya da iyali da kuma mata masu fama da yawan ciwon mara lokacin al'ada ta karshen wata suma baa bar su a baya ba. A takaice dai AG Cera yana temakawa wajen magance cuttukka daban daban wadan ke damun mutum. Domin karin bayani ku tuntuni mu a wannan number +60167474649 ko kuma ku ziyarci shafin mu http://agnutritioninternational.com.* Sai da nai aman na gama sannan ya zuba min ruwa na wanke baki ya fito daga bandakin. Inda na aje Hijab din dazun ya nufa ya dauko ya zo kusa da ni yana kokarin saka min. “Saka muje asibiti” Na bata fuska domin har ga Allah bana jin komai a yanzu, bana jin wani ciwon kai ko wani jiri da zafi jikin kamar na dazun. ““Wallahi bana jin komai Aliyu, aman ne kawai kuma shi ma saboda miyar ne” “Wani abu kika gani a ciki?” “Aa bana son miyar ganye dai?” Fuskar mamaki yai ni kaina ina mamakin kin shan miyar ganye da na ke bayan tana cikin miyar da na ke so, gudun kar Aliyu ya zargi ko bana son cin abincin gidansu ne yasa na ce. “Ba komai yanzu ai na daina jinsa, daman warin manja ne kuma ya daina” Na nufi gurin kular abinci na zauna ya saka hannu ina ci ahankali iyakar dauriya nayi domin har ga Allah yau dai bana son warin manjan nan a kusa da ni wata kila saboda zuwan da mu kai a Las Vegas ne dan sabon da nai a can na wata daya yasa na fara mantawa da abincin naija. “Aliyu ina son tea” “Okay” Ya tashi ya fice rike da wayarsa, yana fita nai saurin nufar bandaki na amayarda da dan abunda na ci na tuwon na wanke bakina na dawo, jinginawa nai da gadon, ina ta tunanin Nana da yadda za tai idan tai arba da mahaifinta. Ba a wani dade ba sai ga Aliyu ya shigi dauke da mug ya zauna kusa da ni ya kai min tea a baki, kadan na kurba shi ma na ji bana sonsa kuma bana son na nuna masa kar yace dole sai munje asibiti, a dole na daure na hanye rabin myg din sannan na kawar da kai sai ya aje kofin ya janyo ni jikinsa ya kwatar ya ciro wayarsa yana lasawa. “A kira miki Nana ko?” Na gyada kai. Be ce min komai ba sai da ya kira Momy suka gaisa ya bani muka gaisa sannan ya sake karba ya ce ta bawa wani a kaiwa Nana wayar ina son magana da ita, yana rike da wayar har aka kai mata ina jin lokacin da suke gaisawa Aliyu har wani kasa yake da kai kamar ba shi, lokacin daya miko min wayar sai ya tashi ya fita daga dakin ya bar ni kadai. “Nana kina nan lafiya?” “Lafiya kalau kun dawo lafiya?” Ina jin yanayin muryarta na san ba kafiya ba, muryarta ya nuna tana cikin damuwa da kuma alamar kamar ta yi kuka ma. “Lafiya Kalau, Nana mun dawo muna Abuja” Ta yi shiru bata ce komai ba. “Nana na hadu da Mai Martaba Sarki Agadaz” Nan ma bata ce min komai ba. “Nana” “Naam” Ta amsa min cikin kuka. “Nana kike yi?” “Idan ban yi kuka ba Ataa mi zan yi? Yanzu haka Yayan yayuna suna nan tare da ni gobe tun da safe sun ce za mu wuce Abuja shi ya bukaci a azo da ni” “Nana har sun iso? Na dauka ma ba ki ji ba” “Da yamma suka zo, amman har yanzu ina ta ganin kamar ba gaske ba, wata kila sai idan na yi arba da shi zan yarda, wata kila ya yafe min wata kila kuma wani abun ne dabam zai fada min, hakika ina kaunar haduwa da mahaifina ina kaunar saka shi a ido ne ko da kuwa idan na je tsine min zai yi, amman Ataa har yanzu ina jin kunya da nauyin abunda na aikata” “Wannan na wuce Nana, ba a iya gyara abunda ya riga ya bace sai dai a tari gaba, ni kaina ina fatar kuma ina tunanin yafiyarce domin ya kirani da jikarsa, jininsa diyar diyarsa, Nana na jidadin ganinsa ko da kuwa wulakanta ni yai ya tozarta ni zan yi farincikin ganin Kakana bayan ke da Lukman da Baba yau ba kara ganin wani wanda yake jinina” “Allahu Akbar” Shine abunda ta fada sai ta fashe da kuka ni ma kukan na ke, mun dauki tsawon lokaci a haka sannan na sauke wayar jin kamar kukan zai yi ma Nana yawa na aje wayar kasa ba tare da na kashe ba. Bayan sauke sallah isha'i Aliyu ya dawo dakin ganin yadda fuskata da ido na sukai ya san kukan nai daman haka na ke idan nai kuka abun baya boyuwa ga farin daya mutum. “Idan har Mahafin Nana ne suka hadu da shi kamar yadda kika fada be kamata ace kina ta damun kanki da kuka kamar haka ba, a tunani farinciki ya kamata ki yi” “Wani farin cikin Aliyu ya yi har sai an koka, taya kake tunanin mace da aka haife ta tun davta tashi bata san kowa na ta ba, rana tsaka ta hadu da kakanta kai tsammanin murna kawai za tai? Mutumen da ganinsa a tare da Nana shine yankewar zubar hawayenta kuma farincikinta, idan har zai yafe mata ya karbe a yadda take yarsa Aliyu ni ma zan koma ya kamar kowa, mai gata ba kuma gata na naira ba gata na yan'uwan uwa da na uba a tare da ni” Zaunawa yai kusa da ni daman tun da muke maganar a tsaye yake ni kuma ina zaune saman carpet din da nai sallah. “Kin ce ba ku da kowa a nan, kin ce ba ki san kowa na ki ba tun da aka haife ki, taya kika gane cewar kina da alaka da wannan mutumen? Babyna mi ya raba ku da danginku? Na dade ina son nai miki wannan maganar amman tunanin sakaki a damuwa ko Mama (NaNa) yasa ban cika damunki ba, kuma ina da burin ko da tsawalla miki da sanin hakan sai na aureki saboda kar na ji wani abu da zai iya zama sanadin da wani a familynki ko nawa zai iya hanani aurenki, na aure ki ba tare da sanin kowa na ki ba sai dan nuna miki tsantsar kauna ni da Momy, Wallahi Ayusher ko da daga sama kika fado zan aureki ba tare da damuwa ba, saboda ke na ke kauna ba wani abun daya shafi dangantarki ba ko kuma asalinki” Kallonsa na ke hawaye taf a idona wata irin kalar kaunarsa da begensa ne ke shiga cikin raina. Hakika Aliyu yayi min abunda ba kowa ne ke yi ba, auren mace da baka san asalinta ba, ko da dan kyauna Aliyu ya aureni yayi min hallacin tun da be taba bayyana hakan ba ya bari a cikin ransa kuma be taba nuna min ba. “Ko da ka tambaye ni asalina a wacan lokacin ko kuma anan gaba idan har wannan abun be bayyana ba, ba zan iya fada maka ba, saboda bana son bayyana abunda Nana ta fada min a matsayin sirrin wanda na san jinsa a gurin wani zai iya haifa mata da matsala ko kuma damuwa” Hannunsa ya kai ya riko nawa. “Kina da karancin shekaru amman kina da wayo da hikima akan dukan abunda ya shafi mahaifiyarki, hakan na da kyau kaunarki na ta karuwa a raina ta ko'ina” Dan murmushi nai ina hawayen da suka ji su tsaya min. Sai ya jani jikinsa ya rumgume ni kuma na lafe abuna kamar ba a bangaren Ammy muke ba, domin na fara sabawa da yanayinsa a yanzu. “Ba ni labari ya kai Mama ta rabu da danginta” Kamar mai karanta labari haka na jera masa yadda komai ya faru kamar yadda Nana ta fada min. Ya tausaya mata matuka kuma ya nuna min jindadinsa da gwarin guiwar cewar Mai Martaba sarkin Agadaz zai yafe mata ta koma cikin danginta ni kaina na tabbatar da hakan domin na lura da yadda ya nuna damuwarsa da ita. “Za mu je mu yi ma Mama Fulani sallama sannan mu wuce gida” Kasa nai da kaina alamar bana son zuwan can. Sai ya mikar da ni tsaye. “Babyna no matter what Mama Fulani zata miki dole ne ke yi respecting dinta matukar kina respecting din Momy da kuma ni” Ban ce masa komai ba, domin ba zan iya fadar wata mummunar kalma akan babban mutum kamar mama fulani ba, ba kuma zan iya aibanta dan'uwan Aliyu a gabansa ba, saboda mijina ne kuma ya nuna min kauna be kama na ci zarafin wani dan'uwansa a gabansa ba ko kuma na fadi wata maganar wacce zata sosa masa rai, duk kuwa da kasancewar ban san alakar da ke tsakaninsa da Mama Fulani ba, ba zan taba son Mama Fulani ba har abada saboda irin kiyayyar da ta nuna min da kyama ita da yayanta sai dai hakan ba shi yake nufin na nuna a gaban Aliyu ba, taya zan kauna ci macw da ya kirani da mahaukaciya, mayya, yar talakawa, yar matsiyata, tai min korar kare a gidan nan, ta hanani taba abun gidanta abinci ma sai da na tara dankwalina ta zuba min, daga baya ta ware min komai nawa dabam kamar wata karya, matar da ta mareni na suma saboda kawai ina rokon ta bar ni na yi mata aiki ta biyani na nemawa mahaifiyata magani? Har abada kuma har duniya ta hade ba zan taba manta wannan ba. Ba ni da zabi daya wuce na bin umarninsa, a dole na bi yo bayansa muka fito tare daga dakin Zee muka sauko kasa inda Ammy take zaune, gaba dayansu kallona suke har Ammy irin kallon na kamar mamaki. “Wani sakamako sai Allah Aliyu, ka auri yarinyar ba dan ka san kowa nata ba, ba dan komai na ta ba, sai ga shi Allah ya maka sakamako da inda baka yi tsammani ba, hakurin da kai da zama da Rahama Allah ya baka wacce ta fita komai” Kamar yadda suke mana kallon mamaki haka ni da Aliyu muke musu shi jin irin maganar da ke fitowa daga bakin Ammy. Zaunawa Aliyu yai a kujera ni kuma na zauna kasa inda Humaira take zaune kasa. “Shiyasa ba a son ka wulakanta mutum ba ka san abunda zai zama ba nan gaba, kuma ba kasan da inda zai iya taimakonka ba, ba dole sai babban taimako ma wani ko alfarma yai maka ya baka ruwa ka sha ai ya jidadin a lokacin da kake jin kishi, waya zai tsammanci ke din jikar babban mutum ce, har ki yi aiki a gidan nan? Ni abunda ban gane ba wai kin san cewa Sarki Agadez Kakani kuwa ko kuma sai yau? Abbah ku ma daya fada min wannan maganar shi kanshi mamaki yake domin abun ya dore masa kai sosai” Ammy ce dai take wannan maganar tana ta kallona. Aliyu ya kalleni sannan ya sake kallonta ya ce. “Ta sani, amman ta yi shiru saboda mahaifiyarta bata son maganar” “Mahaifiyarki ta yi dacen ya Ataa, da baki gudu kin koma cikin dadi kin bar a nan ba, da kuma ba ki saka mata ido har ta wulakanta ba Allah yai miki albarka” Gaba daya suka amsa da amin, ni kuwa tawa amin din a zuciya take, ina jindadin Ammy tun a wacan zaman da nai tana nuna min kauna bata taba nuna min kyama ko kyara ba kamar Mama Fulani, haka ma Muhseen be taba kyamata ba shiyasa na kasa mantawa da shi a zuciyata halinsa kamar na Ammy ne idan ma ba dan fuskarsa da sanin cewar Mama Fulani ce ta haife shi ba idan ka ganshi zaka tsammaci dan Ammy saboda yanayin halinsu na far'a da son mutane ga kuma marhabun da kowa. Misalin tara da yan mintuna muka fito daga bangaren Ammy muka nufi bangaren Mama Fulani, kamar yadda nai wacan karon wannan karo ma baya baya na tsaya Saboda tunanin irin kallon da zata min ko ta fada min wata maganar marar dadi. Shi ya tura kofar falon ya shiga sannan ni ma na shigo babu kowa falon sai tv da ac da ke ta aikinsa. Kai tsaye ya nufi upstairs hanyar dakinta ni dai ina biye da shi har muka isa cikin dakin da na ke sharewa na yi mopping amman a da. Ba Mama Fulani kadai muka tarar ba har da Rukaiya da Maryam da Baby suna zaune dakin, suna ganinmu sukai tsit da alama wata maganar suke tsaka da tattaunawa, ina daga bayan Aliyu ban karasa shigo sosai cikin dakin ba, sai ya matsa gefe ya matso da ni kusa da shi yadda zan bayyana tsundun a cikin dakin. Aiko a take Mama Fulani ta sako min ido tana min wani irin kallo ba na lafiya ba, ba kuma zan bayyana dalilin kallon ko manufarsa ba. “Mama za mu wuce gida” “To Aliyu sai da safe” Ta fada amman idonta na kai har lokacin, sai Aliyu ya kalleni yai min magana kadankadan kamar mai bawa yaro umarni ko kuma mai koya masa abunda zai ce. “Ki ce mata sai da safe Mama” “Mama Fulani sai da safe” Na fada kamar yadda ya ba ni umarni sai tai saurin kawarda fuskarta daga barin kallon nawa da take na tsawon lokaci, ba kuma kawarwa irin ta tsana ko kyama da tsangwama ba, irin kawar nan ta kamar mai tunani ko kuma wanda ya rude ko yake jin kunyarka. Ni na riga juyawa na fito daga dakin sannan Aliyu ya fito ya tararda ni har kusa sauka downstairs din. Ya riga ni isa harabar gidan tun kan na karaso ya janyo motarsa ya bude min front na shiga na zauna na ki rufe ganbun motar da gangan na tsaya ina kallonsa murmushi yai ya bude gefensa ya fita ya zagayo inda na ke ya sumbaci goshina. “Dama ai kin saba bar min mota a bude tun kina budurwa kuma na zo na rufe balle yanzu da kika zama gimbiyata” Ya fada sannan ya rufe motar ya zagaya gefenta ya shiga motar yai mata keys muka dauki hanyar gida. Sai da ya biya ta wani shago ya siya mana kayan zafi da kaza sannan muka isa gida. Da kansa ya fita ta zagoyo inda na ke ya bude min mota ina saukowa ya saka hannunsa ya ruumgumo ni kamar wata yar baby ko kunyar mai gadinsa da ke hangen baya ji, ni kuwa duk kunyarsa ta rufe ni. “Wacan Dattijon Baba fa yana hangenmu” “Sai me dan ya tsinkaye mu? Be san na aure ki ba ni ko kuma be san namiji na taba matarsa ba? Is normal ma ai ba waji abun nai miki ba dafaki kawai nai, kuma shi ai ya saba ganin hakan idan muna tare da Rahma” Ya fada yana bude gidan vaya ya dauko siyayyar da yai mana da dayan hannunsa yayinda dayan hannun yake makalle da ni kamar zan tsire masa. Da hannu daya ya rufe motar muka nufi cikin gidan ni da shi. Ice cream kawai na sha daga cikin abubuwan da siyo mana, domin jin nai bana bukatar komai kuma bana jin yunwa, sai da mu kai wanka ni da shi a tare kamar yadda ya saba min sannan muka saka tufafin bachi muka kwanta. Misalin biyu da wani abu na dare yunwa ta tasheni a dole na bar jikinsa na sauka daga kan gadon na nufi wutar dakin na kunna ko da na juyo sai na ga mutun yana kallona. “Yunwa na ke ji kazar da ka siyo zan ci” Na fada ina dan wara kamar mai jin kunya. “Zauna ba ri na dauko miki” Ya fada yana saukowa daga kan gadon ya fita daga dakin, ni kuma na zauna saman kujerar sai gashi ya dawo da kazar a plate da lemu. Dan karamin tebur ya janyo ya dora plate din sannan ya miko min hannu na taso sai ya nufi bandaki da ni, wani lokacin yadda Aliyu yake min abu kamar wata yar baby abun har mamaki yake ba ni, wata kila saboda baya son yawan magana ne shiyasa ya son ya yi maka abu kawai ba sai ya furta ya ce kai ba wata kila kuma kuanar ce kaiwai yake nuna min. Sai na wanke bakina sannan muka fito na dawo inda na zauna dazun na zauna yawuna har tsinkewa suke kamin na ci kazar. Kusa da ni ya zauna ya saka hannunsa yana bare min yana ba ni a baki ina ci sai da koshi sannan na cige masa hannu da gangan, sai yai saurin cire hannunaa daga baki na dauki nawa yatsan ya kada a bakinsa ya cigeni kamar wani yaro karami, aiko ba shi ri nai ihu saboda zafin da na ji, sai yai saurin rufe min baki. “Shiiiiiiii dare ne” Ya fada kadan-kadan, dariya nai kamar yadda yake dariyar, sannan ya dauko lemun ya ba ni na sha sai ya aje ya matsar da teburin can gefe, ya kwanta saman kujera ya janyo ni na kwanta a kirjinsa, a nan muka kwana har safe yana rumgume da ni sosai a kirjinsa. Bayan mun yi sallah Aliyu ya kwantar da kaina jikinsa yana karatun kur'anin daya saba, ba dade yana karatun ba na tashi daga kwancen da na ke a cinyarsa na sauko falo na nufi kitchen domin samun abunda zan sakawa cikina saboda wata azzababbar yunwa da na ke ji. Freezer na fara budewa sai na ga dukan abunda yake ciki yayi kankara sai na bude dayar da bata aiki na ga Apple da sauran fruits a ciki, apple din na dauko na wanke shi a fanfan kitchen din na soma ci kamar wata mayunwaciya. Ina cikin cikin apple na hudu na ga mutum ya shigo kitchen din da tsage tsage a fuskarsa yana sanye da kananan kayan. Ba shiri na fasa ihu ina ra kiran sunana Aliyu shi ko mutunen sai daga min hannu yake alamar ya kwantar da hankali, tun yana magana da turanci har ya dawo yi da hausa sam ban dauka ma ya isa hausa ba. Da gudu Aliyu ya shigo kitchen din hankalinsa a tashe. “Minenen?” “Wacan mutumen.” Na nuna shi. “Mai mana girki ne” Mai girki sai na ji abu wani iri, namiji da girki to miyasa wacan zuwan ban ganshi ba? Ko da yake kwana kawai mu kai mu ka wuce Lagos. “To ta ina ya shigo?” “Yana da makullin falon ne ko bana nan zai iya zuwa yai girki ya tafi” Ya fada min sannan ya juya gurinsa.. “Abdulgany daga yau za ka daina shigowa cikin gidana nan, Nasir zai tura maka kudinka na wata ba zaka mana girki ba” Risinawa nai ya fara bashi hakuri yana ta rokonsa ya yafe masa idan akan ya ba ni tsoro ne, sai ya fada masa ba dan tsoro ba ne wai yana kishin matarsa ne ba shi da bukatar ganinsa a gidan yanzu. Babu irin magiyar da be yi ba amman Aliyu ya ki saurarensa har sai da ya hada masa da fada sannan ya fice daga gidan. Misalin tara da rabi Aliyu yai mana oder abincin, muna cikin kiran Abbah ya shigo wayrsa sai da suka fara gaisawa sannan ya sanar masa inda yake ya same sa a can. “Yi sauri ki ci Abbah na nemanmu” “Har dani?” Na gyada min kai, da sauri na tashi na bar cin abin ma na shiga nai wanka ina fitowa ya shiga kamin ya fito har na shirya daman can shine ba mai wahala ba ne, shi ma agaggauce ya shirya muka fito tare muka shiga motar. Ba zan iya fadar ungwar da muka je ba, domin ban san ko'ina a cikin garin Abuja ba, sai dai zan iya kwatanta da unguwar manyan mutane domin ta wani bangaren ma tana kama da Las Vegas irin rayuwar nan ta ba ruwa ko da kowa. Gaban wani katon gate Aliyu ya faka tsaya ya danna horn sai ga wasu manya kuma kanttin maza sun bude masa gate din, da sauri na rike hannun Aliyu sai yai murmushi ba tare daya kalleni ba, manyan motoci a cike a gidan na alfarma, bayan motocin ya faka motarsa ya fito ya zagayo inda nake ya bude min na fito daker domin ni gaba daya tsoro ya gama kama ni. Hannuna ya rika ya nufi wani guri da ni da alama shi m be san kan gidan ba, domin kuwa sai da ya kira wayar Abbah ya fada masa mu na waje sai aka turo dogare ya zo ya tafi da mu. Cikin wani irin katon falon muka shiga mai kama da fada, komai na falon mai tsada ne da tsari irin manyan sakuna. Ganin hoton Mai martaba sarkin Agadaz yasa hankalina ya kwanta na fahinci cewar a gidansa ne muke, na yi zaton a falon za mu tsaya sai na ga mun shiga wani falon mai kamar wacan, haka muka wuce falo uku sannan muka iso cikin wani madaidacin falo, a nan na hango sarkin hakimce a akan kujera, babu rawani a kansa kamar jiya sai dai yana sanye da alkyabar sarauta irin mai tsadar nan ga takalmin sarauta kafarsa, Daddy's Rahma na gefe zaune kasa daga dama kusa da Abbah, da sauran jikokinsa, Nana kuma na gabansa kanta a kasa tana ta sheka kuka gwanin ban tausayi da alama gafararsa take nema. Karasawa nai gurin Nana na zauna na dafata Aliyu kuma ya zauna kusa da Abbah yana mikawa mai martaba gaisuwa shi kuma ya daga masa hannu kawai. “Ina jin kunyar ka Mai Martaba saboda abunda na aikata, ban san cewa na aikata babban laifi ba har sai da na rasa a kusa da ni na fara shiga damuwa da bakinciki......” “Shin abunda kika be zame miki darasi ba?” Mai martaba ya tambaya da kansa. “Ya zame min, na rasa komai saboda babu kai a rayuwata, na rasa gata na rasa muhallin, abincin da zan ci sai na yi bara mai martaba, gida gida na ake bi ina rabawa na zauna, har na kai ga wanda aka ga wanda aka wulakanta ni kamar karya, kuma maciji ya tsare ni, Ataa tai ta dawaniya da ni da ta kai ni asibitin sai akai amfanin da rashin kowa na mu aka cire min koda aka sakawa yar wanda ya wulakanta mu saboda rashi, Mai Martaba da koda daya n ake rayuwa saboda rashinka da kuma dangina a kusa da ni, Mai Martaba aka a kulle Ataa a gidan yan sanda saboda ba mu kowa, na rasa na da na biyu da na haifa a gurin baran kudin neman min lafiya, Mai Martaba shin duka wannan ba darasi ba ne? Da ban bijire maka ba da ban ki bin umarninka ba da duka wannan abun be same ni ba, ba ban bata maka rai bada nawa bacin rai be kai haka ba, da ban gudu na barka na bar dangina ba da wani be isa ya wulakanta mu ba” Ta fada cikin daga murya tana kuka sosai nima kukan na ke ina rike da hannunta. “Da duniya tai miki wa'azi miyasa ba ki koma cikin danginki ba?” “Saboda zuciya na fada ba zaka taba yafe min ba, ba zaka taba karbarta ba, masarautar da na saka a kunya na gudu na bari, idan na shiga wahala na dawo be kamata ta karbe ni ba, ban cancanci ko kallon fuskarka nai ba Mai Martaba, amman na barwa Ya ta mawasiya na fada mata bayan raina ta neme ku ta nema min yafeyarka da duka dangina” Shiru Mai Martaba yai na tsawon lokaci kamar baya gurin, falon yai tsif baka jin ko da numfashin kowa. “Ban taba jin na tsani jinina ba, ban taba jin kin jinina ba ko da ko zai kashe wani ya sake kashe wani jinina jinina ne, kuma ina jinsa a cikin jinina..... Bayan neman ki da masarauta tai na kwana biyu, sai na goge sunanki a babin nema har a bada, na bar abunda kika aikata da kuma son ki a zuciyata,... Na yi tunanin idan wahala ta same ki za ki tuna da danginki ki dawo..... Da ace yau mahaifiyarki ta fadi ta mutu da ta mutu da bakincikin da kuma bakincikin guduwa ki barta, babu daren da bata begenki... Idan kowa ya taru sai ta ce kowa yana nan amman ban da Asma'u... Shin kaunar uwa kadai be isa ya saka ki nemi danginki ba......?” Daya bayan daya yake maganar yana kallon Nana. “Ina jin kunyar kaina Mai Martaba, ina ina nadamar abunda na aikata, bakincikin guduwa na bar ku yana nan a zuciyata, kunyar haduwa da ku ta saka na yanke kaunar daga neman yafiyarku a raye har sai bayan rai na, Ka yafe min Mai Martaba ka tausayawa min dan Allah, na sani ko yanzu ina daf da mutuwa saboda lafiyata bata ishe ni ba” Duk da yaren buzanci suke wannan maganar ita da Mai Martaba... Shiru ya sake yi na wani lokaci sannan ya ce a katse. “Na dade da yafe miki Asma'u, na dade da fada a gaban kowa kuma na fada a zuciyata cewar ko ina raye ko a mace na yafe miki duniya da lahira” Da gudu ta tashi taje ta fada jikinsa ta rumgumeshi tana kuka, sai yai murmushi kowa da ke falon sai da tauyasa kuma yai murmushi ban da Daddyn Rahma da baya cikin natsuwarsa. Kuka sosai Nana tai nima nai sannan muka share hawayen mu ni da ita. Bayan komai ya lafa muna kokarin shiga natsuwar mu ne. Mai Martaba ya sake gyaran murya da yaren hausa da baya fita sosai ya ce “Na yi hakan nan ne a gaban ku saboda ku ma ku zama shaida kuma nasan dukanku za ku son jin gaskiyar alakata a Asma'u to yanzu kun ji, ina son kowa ya zama shaida na yafewa Asma'u abunda tai min, Allah ma ka zama shaida na yafe mata duniya da lahira” Tsakanin ni da Nana sai na rasa wa yafi wani farinciki ni ko ita. Daddyn Rahma ya daga hannunsa alamar yana son yai magana da kai martaba sai gumi yake cikin asiri. “Mai Martaba na ce kan sai zancen nema mata hakkinta a gurin Doc Asim na cire mata koda da yai” Kallonsa nai yadda yake maganar muryarsa har rawa take. “Allah sarki ashe rana zata zo irin wannan dakai da bakinka zaka bude baki ka ce a nemawa Nana hakkinta? Bayan duk irin cin mutunci da wulakancin da kai mana? Waenne kalar mutane ba ka turo sun zo sun watsa mana kayanmu sun koramu ba saboda kawai mun raba a kangon gidanka ka ce mu muka janyo maka maciji a gida ka karemu ka wulakanta mu, idan har za a hukunta Doc Asim to har da kai za a hukunta domin kodar da aka cirewa Nana yarka aka sakawa” Na fada cikin kuka. Sai shi ma ya fashe da kuka sosai kamar ba shi ba. “Wallahi Allah ya sani idan na san cewa ku zuri'ar Mai Martaba ne ba zan taba muku haka ba, Wallahi ko shara kuke agidan Mai Martaba ba zan iya wulakanta ku ba, walle har ace jininsa habawa..... Ba hali na ba ne, ko korar da aka muku ni sau daya na fada na ce a fada muku ku nemi wani gurin ku zauna, Wallahi Hajiya ce tai ta turawa aka rakura muku, ita ma kuma basan cewa jinin Mai Martaba ba ne da ba zatai muku haka ba, Wallahi tun jiya da na fada mata abunda ya faru tana can kuka take yanzu haka..... ” Yadda yake kuka abun ko kyau babu domin babban mutum be sha'awa da kuka ballantana shi da yake wani rakeken kato, ni dai sai kallonsa n ake da takaici a raina. “Wanene Doc Asim to?” Jikan Mai Martaba ya tambaya cike da mamaki. Ni kuma sai na amsa masa “Wani ne, wani likita ne wanda na kai Nana asibitinsa lokacin ba mu da kudi sai ya ce zai mata tiyata kyauta ya cire dafin maciji a jikinta ashe yaudarata yai ya cire mata koda, ya bani wata takardar na saka hannu ashe ta siyarda kodar ce ban sani wai saboda ba ni da ilmin komai, sai da ya tambaya ba mu da kowa na ce nasa eh shine ya cire mata koda, haka mukai ta jinya bata warke ba, sai na kaita wata asibiti aka duba aka ce kodarsa ce ya cire na kai kararsa gurin police yasa aka rufeni wai ina son bata masa suna, sanadin hakan Nana ta tashi mutuwa har sai da Allah ya kawo wannan Aliyu ya taimake mu ya kaita asibiti ya ba mu ci da sha da gurin zama” Har lokacin da nake maganar cikin kuka Daddyn Rahma ma kuka yake yi. “Wannan ba tsakanin mu da shi ba ne, tsakaninsa da Shugaban kungiyar likitoci ne” Shine abunda Mai Martaba ya fada a takaice fuskarsa na nuna bacin ransa karara.... *Z A K I -it's not free, pay 300 to 0314795884 Abubakar Gt bank, then send the evidence via 08036126660* *Ina mata son rage kiba? Ina mazan da kiba ta hana su sukuni? Ina masu jikin yai kyau kamar na yarinya? Ina masu fama da kujera ko wani ta bo a fuska? Ina masu fama da hawan jini? Masu diabetic? Ag cera an gwada yayi an tantance ingancin babu shakku ko kadan. AG cera ya zo domin ya temaki garkuwan jiki da kuma lafiyar jiki. Sinadari ne wanda ze magance matsaloli da dama wadanda suke hana garkuwan jiki aiki yadda ya kamata ko kuma yake rusa garkuwan jikin ita kanta.* *Cututtukan zamani daban daban sun sa mutane gaba kuma magance su yana da wahala; irin ciwon Sugar, hawan jini, ciwon sanyin kashi, ciwon gabobi da sauran su. Haka ma cutukka irin wadanda suka shafi fatar jikin wadanda sun hada da kyasfi, pimples, takurewar fata, rakainuwar fata da kuma haske da kyallin fata duka ana shan AG cera kuma yana temakawa wajen magance illolin nan. Mutane masu fama da rashin karfin jiki wajen kwanciya da iyali da kuma mata masu fama da yawan ciwon mara lokacin al'ada ta karshen wata suma baa bar su a baya ba. A takaice dai AG Cera yana temakawa wajen magance cuttukka daban daban wadan ke damun mutum. Domin karin bayani ku tuntuni mu a wannan number +60167474649 ko kuma ku ziyarci shafin mu http://agnutritioninternational.com.* Wani irin sama yake da kafafuwansa yana boxing da hannu kamar wani karamin yaro, sai kuma ya sauko saman gadon ya nufo ni da wata irin far'a ya daga ni sama yana juyawa da ni, kamin ya rumgume. “Oh Allah na” Ya fada yana matseni har ina jin zafin matsar saboda yadda ya rike ni da karfi. “Aliyu minene?” Be bani amsa ba, ya sake ni ya fadi yana sujada, sai kuma ya dago ya ya rike ni yana ta kallon fuskata murmushi ya gama cika masa fuska, hade bakina yai da na shi ya fara min abunda ya saba wato kiss sannan kuma ya cire bakin ya daga kansa kama. “Wayyo Allah na, baby ban san abunda zan yi ba yau, kar na haukace” Har lokacin da yai wannan maganar kansa a sama yake yana kokarin maida ni kirjinsa ya rungume. Ni dai sam ban gane dalilin wannan farincikin ba, da farko ganin layin biyu yasa na tsorata na fara tunanin ko dai ina da wani ciwon ne sai dai yadd Aliyu yake far'a yasa na daina zargin ciwo sai dai kuma ban kawowa raina komai ba, sai mamaki kawai na ke. “Baby i love you, I love you Tomorrow, i love you everyday, i love you so so very much” Na san abunda I love you, da everyday da tomorrow take nufi, kuma na jidadin furtasu a gareni da yai hakan yasa ni na rumgumeshi da duka hannayena, ina jin kamar nima na fada masa haka kuma ina jin kunya. Ji nai ya dago kaina yana ya sumbatar ko'ina a fuskata da jiki kamar mahaukaci sai kuma ya sake rumgume, sake ni ya sake yi fara rawa a gurin yana jujjuyawa kamar wani mace, sai kuma ya rikoni yana cilastani ni ma nai rawar. “Very Very soon Baby za ki zama uwar Baby” Ya fada yana rike da fuskata har da wani turo min bakinsa yake kamar nai yi yarinya karama magana da zolaya. Uwar baby kuma ban fahimce shi ba. “Kamar ya” Juyar da ni yai ya zamana bayana ne a kirjinsa sai ya saka dayan hannunsa yana shafa cikina. “Kamar haka, idan kin haihu” Zaro ido nai sai yanzu na gane komai barobaro da sauri ya juyo. “Ina ciki kenan?” Juyar da ni yai ya rungume. “Muna da ciki dai Baby not just you, ko ma na ce ina da ciki Baby i love you” Ya fada saitin kunnena. Sai na fashe da kuka. “Aa yanzu kowa sai ya san abunda ya faru ko? Idan aka gan ni da ciki” “Daman ai an san dole wani abun zai faru” “Amman dai akwai kunya kuma ciki da wahala” “Ba wani wahala, kunya kuma ai tunda kika yarda kika zauna gidan miji ta wuce” Ban san dalilin rashin jindadin cikin ba, sai ma tsoro daya kama ni yo ni ya ma zan yi na haihu? Kuka na fara bana wasa ba tun yana rarrashina a hankali har abun ya koma bashi tsoro. “Haba Babyn wannan fa abun farinciki ne, wannan shekarar ina cikin ta tara da aure amman ban samu haihuwa ba sai yanzu, Momy Mama Fulani Abbah Daddyn da duk family and friends da sisters idan suka ji dadi za su ji kuma su so ki sosai” “A a nidai ba yanzu ba nidai bana ma so gaba daya” Zaunar da ni nai saman gadon ya zuba min ido yana ta kallona. “Dan girman Allah Babyna ki daina kukan nan, kar kukan ya cutar da abunda ke cikinki” “Ba zan iya iya kallon kowa ba idan nai ciki, kuma ba zan iya haihuwa ba” “Ciki ai kin riga kin yi, yi hakuri ba za a sake wani cikin ba” “Da gaske?” Dariya yai ya gyada min kai. Sannan na sausauta kuka shi kuma ya tashi yaje debo min ruwa. Yana fita na daga rigata na leka cikina sa nai sauri na rufe. ALIYU POV. Ya sauko downstairs wayarsa a hannunsa yana kiran Nasir, wannan karon be jira Nasir ya fara magana ba kamar yadda ya saba yana kiran daukar kiran Aliyu ya ce “Congratulations to us na kuma zama Daddy nima na yi ajiya a cikin Ayusher” “Wowooooooooooooo Aliyu are you serious? Oh my God” “Na rantse da Allah Nasir har ban san irin farincikin da zan yi ba, na rasa abunda zan yi Wallahi ji na ke kamar na hadeye Ayusher a yau” “Wannan abun murna ne a garemu gaba daya ai, amman Momy ta ji da Mama Fulani?” “Ban fadawa kowa ba sai kai, nima yanzu na ga result din” “Ni zan yi musu albishir karka ce zaka fada musu na san baka da kunya” “Ai na zancen kunya a nan Nasir, wane irin kunya a gurin farinciki? Ai ba wannan zancen shi dan na fada na ce tana da ciki kuma wani abun kunya ne? Ita ma yanzu ta gama kuka wai idan suna ji zata ji kunya” “Ai kai ba saka gane ba ne saboda ka saba yin abu normal ne” Murmushi Aliyu yai ya kashe wayar, har ga Allah shi be ga abun kunya a fadar matarsa ta yi ciki ba, shi ba duk abunda ya san idan ya aikata ba haramun yai ba to be ga abun jin kunya a ciki ba, da dai zina ya aikata ko wani alfasha shine abun jin kunya, domin shi ya fi dacewa ka ji kunyar Ubangijinka sama da na kowa. Freezer ya bude ya dauko ruwan gora ya zuba sai da ya sha dan ya ji yanayin sanyinsu kar su cutar da abun cikinta sannan ya sirka da wasu ruwan sai ya dauko kofin ya dawo dakin da take. Inda ya barta a nan ya same ta zaune da kansa ya kai mata ruwan a baki yana bata a hankali har ta sha rabin kofin sannan ya aje ya zauna kusa da ita ya zuba mata ido. Be san abunda zai mata ba, rumgumatar ba zai wadatar da shi ba, kallonta ba zai wadatar da shi ba, saurarenta ko yi mata wani abu ba zai wadatar da shi ba, yana jin cewar hadeye ta kawai zai yi ta zauna tana cikin cikinsa ita da abunda ke cikinta sannan hankalinsa ya kwanta sai dai kuma babu wannan damar ya rasa inda zai sakata tsabar farinciki. Haka yai zaune ya sakata a gaba har aka kira sallah la'asar sannan ya sumbaci goshin nata da cikin ya fita zuwa masallaci, daga masallacin ya wuce restaurant ya siyo musu abinci, ya so ya kira ya tambaye ta abunda take so amman babu yadda zai yi tunda bata da waya. After restaurant ya wuce wani babban shago ya siyo mata sabon phone mai tsada wacce ake yayi sannan na nufo gida, ko da ya shigo ya ji motsinta a kitchen sai ya nufi kitchen din kai tsaye taliyar indomie ya tarar tana zubawa a plate tana murmushi. “Yunwa na ke ji sosai shi ne na dafa indomie” Ta fada masa ganin ya tsaya yana kallonta da murmushi. “Wow yau Gimbiyata ta yi aiki da kanta bari na dan dana na ji, ashe kin iya girki ko?” “Eh na iya tuwo na iya dafaduka na iya dafa taliya na iya sararafa kanzo na iya shimkafa da miya kuma na iya da wake, amman ban iya amfani da wacan abun ba sai na daka a turmi” “Wow amman dai ai ba sai kin yi aiki da yawa haka ba” Ya karasa kusa da ita yana rike da ledodin a hannunsa. Fork ta dauko ta saka ya debo taliyar sai ya busa masa a bakinta sai da huce sannan ta kai masa a baki, luma daya ya rumtse ido saboda wani azababen yaji da ya ji, da sauri ya aje ledodin hannunsa ya dauke plate din. “Wallahi ba za ki ci wannan abincin ba” “Mi yai?” “Wannan uban ya jin?” “Ji nai ina son ya ji shine an cika kadan” “Wannan cikin be wani kwari ba za ki ce za ki ci wannan yajin, noooooo ga wani abincin na siyo miki ai zo mu ci tare” Ta mairairaice fuska. “Haba Aliyu ina so Wallahi” “Haba Baby ki tausaya min mana” Aje plate din yai gefe ya bude dayar ledar mai waya ya dauko ya mika mata. “Ga waya ke ma ki fara bugawa kina daukar hoto” Ba shiri da zaro ido ta karbi wayar da sauri da daka wani irin tsalle kamin da dire yai saurin cabeta. “Ke yanzu fa ba ke kadai kike ba, ki daina irin wannan abun” Ina bata ma jin me yake fada sai ihu take ya rumgume shi sabar farinciki har da yi masa kiss a fuska. “Na gode na gode na gode na gode na gode na gode na gode na gode na gode na gode na gode na gode na” Haka tai ta maimaitawa sai da ya rufe mata baki, sai kuma ta fashe da kuka kuka irin sosai din nan kamar wacce akai wani abu rasa tai me zata yi, ita a rayuwarta bata taba rika waya ba ko karama balle babba irin wannan mai screen kato. Rikota yai suka baro kitchen din suka dawo falo suka zauna, sai ya karbi wayar ya bude mata ya hada mata. “Idan na fita ko kuma zan saka Nasir ya siyo miki layi mai kyau na ki na kanki, kuma yanzu sai an saka wayar carji idan ta yi full sai a fara tabawa” Ta yi saurin tashi daga kan kujerar tare da carjar wayar ta nufi socket ta saka ta zauna s gurin ta tsare wayar. Shi kuka ya tashi ya koma kitchen din ya dauko musu abincin daya siyo musu ya zo kusa da ita ya zauna ya bude abincin. “Aliyu ka dauko Nana na nuna mata wayata” “Ba yau ba dai, gobe ai zamu je mu gaisheta sai ki nuna mata” “Har sai gobe” Ya gyda mata kai yana deban abincin ya bata a baki, jin tai bata gamsu ba har sai da ta dawo saman jikinsa ta zauna ta rumgume. “Na gode sosai Allah ya kara arziki ya tsareka daga dukan sheri Allah ya biya maka bukatunka na alheri” “Nima na gode da ki kai ciki” Rankwashinta ya ji a kanta ya ji kamin ya ji sautin dariyarta yai murmushi ya kara rumgume ta. Ba wani abun kirki ta ci ba abincin tsabar zumudin waya ya saka ta manta da wani zancen cin abinci duk kuwa da tana jin yunwar. Ranar a gaban wayar ta kwana duk yadda ya so ta dawo ciki daki su kwanta kin tai tana ta jiran har sai wayar ta yi full sannan ta fara tabawa, a dole ya dauko matashin kai ya aje a gurin yai mata matashin kai da hannunsa ya lulluba musu mayafi suka kwana a gurin har safe. MAMA FULANI POV. Tun da Abbah ya dawo ya fada mata abunda ya faru kuma ya ce mata Mahaifiyarta Ataa zata zo kuma a nan zata sauka sai ta fasa inda zata saka kanta sabar kunya, dole ne tai mata tarba ta musamman kasancewar yar sarkin Agadaz sai dai taya? Baya ta wulakanta yarta? Ta sani har abada ita da Ataa ba za su taba ganin kimarta ba, yadda za tai ido biyu da ita ma take tunani. Gabanta be kara faduwa ba sai da ta ji tsayawar motar Aliyu da sauri ta tashi ta shige dakinta har da hadawa da gudu. Saman gado ta haye ya lulluba da blanket tana jin sallamar Aliyu ta fara rawar sanye abunda bata taba ba a rayuwarta. “Mama ba ki da lafiya ne?” Ganin shi kadai ya shigo yasa ta tashi zaune cikin yanayin damuwa tana kallonsa ta ce. “Aliyu ina jin kunyar hada ido da Ataa da mahaifiyarta, ba ni da wannan idon na kallonsu ko na ce zan musu wata magana, waya taba tsammanin haka Aliyu? Ko daman can ka sani?” Zaunawa yai kusa da ita cike da damuwa da damuwarta domin ita din ma uwarsa ce kuma mai damuwa da abunda ya dame shi. “Ban sani ba Mama ban ma taba kawo wa a rana cewar wata wana haka zai faru ba, iyakar abunda na rike wata rana dole yan'uwanta za su bayyana, amman ban taba kawowa kaina cewar masu kudi ba” “Ka huta, Momy ma bata mata komai ba sai ni oh ni Fulani yau na jin kunya na shiga uku, Wallahi ko a mafarki aka fada min cewar wata rana yarinyar zata zama haka ba zan yarda ba, amman ji abunda ya faru? Ina ta zagin yarinyar nan ina ta ci mata mutunci ashe ma har ta fi mu komai” “Mahaifiyarta tana can falo, Ayusher kuma tace zata tsaya bangaren Ammy” “Eh ta tsaya can ai tana gaskiya, ni ai muguwa ce na san haka take kallona, ka ji fa rashin rabo jiya na hana yarinyar ruwan sha a gidan nan ashe ashe.... ” Wannan karon har da kwalla gaba daya duniyar ta rikice mata, domin yadda take son zuri'ar masu hannu da shuni da ace ba tai wa Ataa haka ba da yanzu sai ta kulla abota da Nana, kuma ta sake jikinta da ita amman ina ta bata komai. Tashi Aliyu yai ya fice daga dakin, ya barta ita kadai tana da tufka da warwara, har da dan lekowa ta leki fuskar Nana ta koma cikin dakin, gaba daya kunya take ji kamar wacce tai sata ko. Maryam ce ta shigo cikin dakin sai Mama Fulani ta juyo da sauri ta kalleta. “Ke kin gaishe ta?” “Eh na gaishe ta ni da Rukaiyah” “Ta karba miki?” “Ta karba mana amman tana ta kallonmu” “Kunyar sauka na ke ji” Ta fada gumi na karyo mata. “Wallahi Mama da kunya wa ya saka ran haka zai faru? Kara ma Ammy bata taba mata komai ba, ita da Ya Muhseen da balle Ya Aliyu da yake mijinta gaba daya” Mama Fulani ta dora hannu saman kai. “Kai ni dai kan na shiga uku naga ta kaina, ni yanzu ya zan yi na fita na ganta?” “Ai ita bata san ki ba, kuma kin san Ataa kila ma bata taba fadar abunda kika mata ba, kuma ai dole ki fita tunda Abbah yasa an kawo ta nan” Babu yadda Mama Fulani ta iya da abunda ya fi karfin wuta, dole ta kulle kunyarta a baren zane ta fito tana saukowa a hankali. “Lale lale mara da Hajiya ashe har kin iso da yake ina wanka ban san shigowarki ba” Ta fada tana dariya da far'a kamar ba ita ba, Nana kan kallonta kawai take har ta zauna saman kujera tana gaisheta kamar zata risina. “Hajiya Ina wuni? Ya gida ya hanya?” “Lafiya kalau Alhamdulillah” Nana ta amsa a hankali ba tare da ta saki fuskarta ba. “Aa ya ba a kawo mata komai ba? Ke Rukaiyah me kike yi baki kawo mata komai ba” “An kawo mata ruwa da lemu ta ce a dauke wai ta koshi” “To ko kin fi son na gida irin wanda ake hadawa wannan?” “Bana jin kishin ruwa ko yunwa a yanzu, ki ce Fulani?” Mama Fulani ta ji kamar ta nitse cikin kasa. “Eh ni ce, ai ni ce na rika Aliyu a hannuna na girma tun yana dan yaye, ai shi mai gidan nan mijina shi da mahaifin Aliyu uwa daya uba daya suke, mijina shine yaya sai mahaifin Aliyu ne kane, da yake a wacan lokacin ni da Momy a makaranta kawayen juna ne sosai tare mukai karatu a ABU zariya, mahaifin Aliyu dan'uwanta ne sun hada kakanni daya kuma......” Ganin Nana ta zuba mata ido sai ya saka ta ji kunya har da yin kasa da kai. “Ataa na yawan ba ni labarinki ai” “Ehhh Wallahi ni ce fa Mama Fulanin dai, Allah sarki Ataa baiwar Allah, Wallahi Ashe abun haka ne, Wallahi ehh huh” Mama Fulani sai kame kame take cike da kunya. Sai ta mike tsaye ta nufi kitchen. “Ban ma dora girkin rana ba da yake bana dan jindadi, Rukaiya ki kaita gurin Ammynku su gaisa kamin na gama abincin, sai dai ban sani ba ko kina da ra'ayin wani abun da za a dafa miki?” “Aa” Nana ta amsa tana mikewa tsaye ta bi bayan Rukaiyah wacce tuni ta nufi kofa, sai da ta fice Mama Fulani ta fadi zaune a kofar kitchen ta dafe kanta. “Wai ni Allah wannan abun be min dadi ba, ai dai kam ba zata ci komai nawa ba, tun da yarta zata fada mata cewar na hanata ita, ai idan da kunya ni ma ba zan ce zan bata ko?” Magana take kamar mai yi da wani gaba daya abun ya dameta a yanzu, wacce suke wulakantawa suna gani ba komai ba, yau ta koma sama da su, a cikin arzikin kakanta suke tsoma ludayinsu su ci. Kamar kallon yadda Ammy take da far'a haka ta amsa mata sallamarta tai mata lallen marhabun, sai a lokacin Nana ta dan saki jiki har tai murmushi Rukaiya sai kallonta take ganin ta sakewa Ammy, kamin ta juya da fita. “Aiko yanzu yanzu nan Aliyu ya fita tare da Ataa” “Allah sarki ke ce Ammy ko?” “Eh ni ce Allah dai ya sa lafiya?” Ammy ta fada tana dariya sai Nana ita ma tai dariyar. “Lafiya kalau labarinki na ji a gurin Ataa, har da kowa da wa yaranki” “Allah sarki ina ruwan Ataa, yaran duka basa nan sai Humaira ita ma yanzu ta fita ko bangaren Hajiya Fulani tai ban sani ba, ya gida ya hanya?” “Alhamdulillah” Ammy ta shiga ciki ta kawo mata ruwa da da dan abun tawa, a nan kam Nana ta sha ruwa har da cin abinci ma domin ita ta gama nata abincin rana tuni, Mama Fulani ma abunda ya faru ne yasa jikinta yai sanyi har taji kamar bata da kuzarin girkin. Mama Fulani na zaune bakin kofar kitchen din tana jimami sai ga Rukaiya ta dawo tana labarta mata cewar Nana ta sake a gurin Ammy har da dariya. Mama Fulani dai abun duniya ya isheta ta bata ce komai ba sai domin ta san duk abunda akai mata bata da bakin magana a yanzu kuma ta cancanci fiye da hakan ma. Maryam ce ta fito rike da wayarta ta sauko kasa ta kawo mata. Ganin number Nasir yasa tai saurin picking. “Mama ina wuni?” “Lafiya Nasir ya gida” Ta amsa da muryarta kamar ba ita ba. “Lafiya Kalau Mama kira nai na miki albishir kamin kowa ya riga ni” Gabanta ya fadi domin a halin da take yanzu tsoron jin komai take. “Albishir kuma?” “Eh Ataa ce bata jindadi Aliyu ya kaita Asibiti shine suka ce ciki ne” Dif Mama Fulani tai daukewar wuta, ta zaro ido ta mike tsaye da sauri sai kuma ta cire wayar daga kunnenta ta duba mai kiran ta ga Nasir din dai ne ta sake mayarwa a kunnenta sai idonta ya cika da kwalla. “Allahu Akbar, Allah mai iko Allah sarki” Ta kashe wayar sai ta koma saman sofa ta zauna sai hawaye suka fara mata sallama. “Lafiya Mama? Miya faru?” “Wai Ataa tana da ciki, kiji wani al'amari daga Allah, duka abubuwan nan sun zo mana ta hanyar da ba za mu iya nuna farincikinmu ko kulawarmu ba, a da idan wani abun farinciki ya samu Aliyu ni yake fara yi ma albishir kamin kowa, amman yau ya fadawa Nasir wannan albishir din bayan ya san na fi kowa bukatar ya samu haihuwa, be fada min ba saboda yana tunanin bana son Ataa ba zan yi farinciki da samun cikin ba, Innalillahi wa'inna ilaihirraji'u” Tashi tai jiki ba gwari ta nufi dakinta, zazzabi ne ya rufe ta gaba daya yamma cin batai shi da dadi ba, da ada ne da yanzu ta fara kiran Momy da duk wani makusancin da labarta masa abun dadi da murna ya samu amman yanzu babu wannan damar, da dare ma kasa runtsawa tai tana son ta kira Aliyu ta yi magana da shi amman tana jin nauyi saboda ta san yana tare da Ataa, kuma tai ta jiran ya kirata be kirata ba har garin Allah ya waye. Misalin bakwai na safe tana zaune saman carpet din da tai sallah kasancewar jiya da yau ba ita ce da girki ba Ammy ce, Nana kuma ta kwana a bangaren Ammy, ban da Maryam da Rukaiya babu wanda ya san bata jindadi domin Muhseen be shigo gidan ba gaba daya tun da ya ga Ataa ta zo ya sake fita be dawo ba. Wayar Aliyu ringing biyu ya daga da far'asa yai mata sallama. “Assalamu Alaikum” Ta amsa mishi da muryar mai karantar da shi damuwarta. “Aliyu kana tunanin ba zan yi farinciki da samun cikin ba shiyasa baka kira da kanka ka fada min ba?” “Wallahi ba haka ba ne Mama Nasir ne ya ce kar nai rashin kunya na bari zai kira ku ya fada muku amman ba dan wani abu ba” “Aliyu yadda na ke son ka haihu ko da karuwa ce ta samu ciki da kai zan yi farinciki, saboda na ce bana son Ataa ba shi yake nufin bana son abunda zata haifa maka ba, ita ma kuma da na san da zuwan wannan abun da ban aikata mata komai ba, ina jin kunyarta da na mahaifiyarta na abunda na aikata musu, amman Wallahi ba zan taba kin jininka ba ba zan taba tsana ki nuna kyama a gurin abunda Ataa zata haifa maka ba, ko da ko ace gaskiyar wacece ita be bayyana ba” Tana gama fadar hakan ya kashe wayar tana hawaye. ALIYU POV. Damuwa ce shimfide a fuskar Aliyu, yadda ya ji muryar Mama Fulani abun be masa dadi ba, yadda baya son wani abu ya dami Momy haka baya son abunda ya taba Mama Fulani. “Minene?” “Mama ce, bata jidadin yadda na sanar da Nasir zancen samun cikinki ban sanar mata ba” Ataa ta aje mug din dake hannunta na tea da ya hada mata tun da azuba tana kallonsa. “Bata jidadin na samu cikin ba? Ko kuma saboda ni ce na samu cikin yasa ba ta jidadi ba?” Matsowa yai da ita kusa da shi. “Mama tana son cikin nan, ko da ko ke ko wata ce wadda ta fiki talauci, ko kuma wacce ta fiki arziki, saboda tana son farincikina, kuma tun kamin Momy ta fara damuwa da rashin haihuwa ta, ita ta fara min zancen karin aure kamin Momy, Mama Fulani bata son wani abun da zai taba ni ko kadan, shiyasa ko a wacan lokacin da na ake fada mata cewar ni ne da matsalar ba Rahma sai ta nuna damuwarta kuma ta nuna min na kara aure idan ban haihuwa sai a barwa Allah ko kuma a cigaba da neman magani” “Kana da wata matsala ne?” “Ba ni da wata matsala, Rahma ce mai matsala domin kwa haihuwa baya iya zama a cikin mahaifarta, amman sai na boye mata, da farko wace na ke ni d ita duka ba mu da matsala sai na biya likita kuma na roke shi ya fada mata haka, saboda kar damuwar tai mata yawa, ga ciwonta kuma idan ta ji bata iya haihuwa abun zai nata yawa, daga baya na maida abun kaina na ce mata da kowa cewar ni ne mai matsala ba ita ba, saboda Nasir ya ba ni shawarar yin hakan” “Amman Aliyu miye alakar da Mama Fulani? Na san Momy ce ta haife ka” “Momy ce ta haife ni tabbas, amman a hannun Mama na girma, Mama Fulani da Momy aminan juna ne tun a makaranta a lokacin Mama Fulani tana Yola kasancewar ta yar can, Momy kuma yar sokoto amman sai suka hadu a ABU zaria gurin karatu a daki daya suke komai tare suke kamar yadda na samu labari, Daddyn dan'uwan Momy ne Cousin brother dinta ne ta gurin uwa, tun tana makaranta ta fada min wani lokacin a sokoto suke hutu ita da Mama Fulani, wani lokacin kuma a yola suke hutu gidansu Mama Fulani, after sun gama makaranta aka saka ranar aurenta da Daddy, a gurin bikinsu ne Abbah wanda yake kanen ga Daddy ya ga Mama Fulani har ya fara sonta har Allah yai abun ita ya aureta, a sokoto suka zauna dukansu a wacan lokacin shiyasa a lokacin da Momy ta haife ni na isa yaye sai Mama Fulani ta yayeni, daga nan Daddyn ya samu aikin wannan kamfanin suka dawo a nan Abuja sai ta dawo tare da ni, kawaici irin na Momy ya sa ta kasa cewa a bata danta domin har tsawon lokacin da na fara wayo Mama Fulani bata samu ciki ba, sai daga baya aka haifi Muhseen daga shi kuma sai ta dade kamin ta sake haihuwa wanda hakan yasa Abbah ya auro Ammy, sai kuma haihuwar ta zo mata daga baya su kai ta yi tare da Ammy. Mama Fulani ta rike ni tsakani da Allah bata bari wani abun ya same ni ko nai kuka duk wani abun da nake so shi take min, kina da idonki idan wani abun ya shiga tsakanina da Muhseen ni take ba gaskiya, ko da shi ne da gaskiyar, bata taba yarda yaranta su rainani shiyasa na taso bana sake musu fuska saboda kar su raina ni din, har abun ya zame min jiki, kowa a gidan yana saunata ko yin wani abu a gabana ciki har da shi Muhseen din, hakan yasa ba mu jituwa da shi, ba ma san inuwa daya bama fahimtar junanmu, saboda shi yana ganin ina akan kuskure abubuwan da na ke yi ni ma kuma ina ganin yadda yake sakewa yana wasu abubuwan basa burgeni, a ciki kuwa har da tsanar talaka wanda na samu asalinsa daga gurin Mama Fulani, ban taba daukar cewar abunda Momy da Muhseen suke nuna min abu ne mai kyau ba sai haduwa ta da ke” Yayi shiru sannan ya rumgume ya sumbaci saman kanta. “Na san ba za ki taba son Mama Fulani ba, amman zan jidadi idan kika aje kiyayyarta a zuciyarki ba tare da kin nuna mata a gabana ba, Mama Fulanu tana da muhimmanci da daraja da kima a gareni wanda Momy ma ba zata so ki wulakantata ba, Mama tana son cikin nan ko da ko bata so ki ba saboda cikin jikinki nawa ne, tana jin kunyarki da mahaifiyarki da tasan da zuwan wannan abun tace da bata aikata miki komai ba” “Miyasa sai ni Aliyu? Wata kila da asalina be bayyana ba, da har yanzu Mama Fulani ba zata ce tana jin kunyata ba, ko ba ni ba ko wane dan'adam mai daraja ne Aliyu, idan babu talaka wallahi masu kudin ba za su iya rayuwa ba, da babu talaka fada min wa zai zo gurinta nema har ta gane cewar tana da arzikin? Wa zai gina mata gidan da zata zauna? Wa zai tuka mata motar da zata hau? Wa zai mata wanki da guga da gyaran gida ko na sani abun idan ya kama? Wanda ba shi da jinkai yake so da kauna da tausayi ba kyara da tsangwama ba, abun Alfarinka ne ace yau kana da abunda zaka iya dafawa ka bawa wani ko kuma ya taimaki wani a cikin taimakon da Allah yai maka, tarin dukiya ba abun alfahari ba ne tarin imani da yawan taimako da kyakkyawan aiki shine abun tinkaho da bugun gaba, ranar lahira a wareka a bainar jama'a a karramaka akan aikin alherinka shine abun jindadi, ba a tsare ka ana tuhumwar ka da daga inda ka samo dukiyarka ba kuma taya ka kashe ta? Wa ka zalinta da ita waya amfana da ita? Wani aiki kai ita saboda Allah? Aliyu ya zaja ji idan Allah ya tsayarda Mama Fulani a gabansa ya tuhumeta akan zalincin da tai na wani ko musgunawa saboda ita tana da dukiya shi ba shi da ita ba? Wanda ya baka dukiyar da kansa ya tambayi ka dalilin wulakanta wani saboda abunda ya baka shi ya hana shi? Miyasa ba zaka fada mata gaskiya ka nuna nata abunda take ba daidai ba ne? Talaka kan kaurai zai dade da shiga mai kudi yana can yana amsa tamaboyoyin dukiyarsa, ashe ko dukiya da zata saka ka fadin rai da wulakanta wasu ba abun tinkaho ba ce matukar ba ta taimakon bayin Allah ce da addininsa ba” ATAA POV. hawaye na ke yayinda na ke maganar ba da Mama Fulani kadai na ke ba, har da Aliyu na ke domin shi ma rayuwarsa kenan kamin yanzu, da kuma duk wani mai halin irin nasa. Yadda na ga jikinsa yai sanyi sosai ya karantar da ji cewar sakona ya isa a inda nake son isar da shi domin hawaye na gani a idonta yana ta kallona. “Na gode Allah daya bani mata kamar ke, yarinya ce ke amman mai hankali da natsuwa da hangen nesa, ina son ki ina son abunda cikin cikinki” Ya fada yana murmushi. Hannu na saka da kaina na share masa hawayen na rumgume shi da kaina ina jin wani irin dadi marar misaltuwa. RAHMA POV. Kamar yadda ta yanke shawara samun Daddy ta ta fada masa cewar zata koma dakin mijinta sai ta fara samun Mommy da zancen a lokacin Mommynta na jimmamin al'amarin da Daddyn Rahma ya fada mata a waya wanda ya hana shi dawowa. A jiya kamar yadda yai alkwari. “Mommy ba ki ce komai ba” “Mi zan ce Rahma? Anya ma Aliyu zai kalleki ma yanzu kuwa?” “Me kike nufi?” “To ya samu wacce ta fiki komai” Raham ta saki baki jin irin maganar da mahaifiyarta take da kanta. “Mommy ke da kanki kike fadin wannan maganar? Ko kin manta wacce Aliyu ya aura ne?” Mommyn da juyar da fuska cikin damuwa. “Bana son fada miki abunda zai zame miki tashin hankali ne” “Minene dan Allah fada min” “Kin san sarkin Agadaz wanda ya zo?” Rahma ta gyada kai cike da son sani. “To kakanta ne, duk uwar dukiyar da muke tinkaho da ita ta gidansu ce, ke kiji wani al'amari” Rahma ta girgiza kai. “Mommyn kin gane me kike fada min kuwa?” “Aifa sai ki yi, yanzu haka Daddynku na can gurin sarki ya fada min ya sha kuka jiya har idonsa ya kumbura saboda Ataa ta fadawa Mai Martaba abunda mu kai musu” “Innalillahi wa'inna ilaihirraji'u Innalillahi La'ilaha illallahu Muhammadu Rasulullah Sallalahu Alaihi Wassalam, jama'a Mommyn da gaske ko karya? Taya to taya how how how Mommy” Ta fashe da kuka ta mikewa tsaye sai Mommyn tai saurin riketa. “Ke ke saurara kwantar da hankali” “Taya zan kwantar da hankalina Mommy fada min taya ya zama kakanta taya? Wallahi hakan ba zai yiyu ba, sai dai idan wata Wallahi ba ita ba” Zaunar da ita Mommyn tai ta jera mata komai dalla dalla kamar yadda Daddynsu ya fada mata a waya domin ya fada mata cewar ba zai dawo da wuri ba sai Mai Martaba ya koma da ko rakiyarsa kawai zai yi Abuja ya dawo. “Wayyo Allah na na shiga uku Mommy mutuwa zan yi yau, wayyo zuciyata wayyo kirjina wayyo raina” Faduwa tai kasa tana da kuka da ihu kamar an mata mutuwa. Gaba daya yan'uwanta sai da suka taru a dakin suna ta jimamin al'amarin gaba daya abunda suke tunani Mai Martaba zai iya kwace duniyarsa daga hannun Daddyn gaba daya cikinsu ya duri ruwa. Haka Rahma ta kwana ta wuni tana da aikin kuka da tunani kala kala ada ya tsara yadda za tai zaman kishi da Ataa saboda tana yar talakawa to yanzu kuma ba ta san irin zaman da zatai ba. Washe garin ranar da Daddyn ya dawo duka suna zaune falonsa dukansu suna cikin damuwa har shi domin Mai Martaba ya kama hanyar zuwa jigawa tun jiya ba tare da shi ba, kuma be ce komai akan abunda Ataa ta fada am mata ba, shine abunda yakr ta ba Daddyn Rahma tsoro. “Ni wannan abun har mamaki yake ba ni, abu kamar a mafarki” “Ai ba ki san a mafarki ba sai da yarinyar nan ta fara fadin abubuwa a gaban mai martaba kaina kamar ya tsare, kunya ta rufe ni ai ban san lokacin da fashe da kuka ba” Cewar Daddyn Rahma bayan Mommyn ta fadi nata. “Baku tunanin abun nan zai min yawa da kuke ta maganganun nan a gabana? Tun da na tashi lafiya bata isashe ni ba, ga auren da Aliyu yai yanzu kuma yarinyar nan azo ace wai cikin dukiyar gidansu muke rawa da tumami, haba Daddyn haba ba a kyauta min ba” Ta fashe da kuka, Ikram ta ce. “Haba Rahma ya za ki yi da ikon Allah? Kullum idan ina fadar cewar abunda ake a gidan nan ba a kyautawa tun daga kan mijinta da kuke biyeta tana juya shi yadda ya zo da kuma yadda kuke yi ma mutane sai kuna ganin laifina kuna ganin ban kyauta ba ko kuma ni ban gane kan dawon garin ba, yanzu ai wa gari ya waye? Tsakani da Allah Rahma ciwon nan na ki tsoron Allah ya kamata ya Kara miki, ciwon kadai ya isa ya saka ki fahimcin cewar dukiyar ba komai ba ce tunda ta kasa baki dauwamammiyar lafiya ko ta hana ki ciwo ko mutuwa, wani yana can da talaucin amman lafiyarsa kalau hankalinsa kwance yana cikin farinciki” Mommyn ta daka mata tsawa. “Haba Ikram yar'uwarki kike fadawa wannan maganar? Ba zaki barta ta ji da abunda yake damunta ba?” Rahma ta mike tsaye tana hawaye ta nufi dakinta, saman gadon ta fada ta kwanta tana wani irin kuka kamar ranta zai fita, tana jin wayarta na ringing ta ki ta daga sai da ta sha kukanta ta koshi sannan ta shiga bathroom ta wanke fuskarka ta fito idonta sun yi ja sosai kanta har wani haukan ciwon yake. Wayar ta duba ganin number Aslamiya matar Nasir yasa ta kira ta tasan ba zai wuce ta labarta mata cewar ubangidan Daddyn kakan Ataa ne ba. Sai dai a lokacin da ta dauki wayar bayan sun gaisa sai labarin ya sha banban ta labarta nata cewar Ataa na da ciki. Wani irin abu Rahma ta ji kamar tana zaune a saman kaya, ta mike tsaye sai ji tai dakin na juyawa mata bata san lokacin da wayar ta subuce daga hannunta ta fadi kasa ba, cikin jirin ta fara takawa ta nufi kofa tana fadin Innalillahi wa'inna ilaihirraji'u, so take ta fita taje gurin da sauran yan'uwanta suke kar ta rasa ranta a dakin ita kadai. Kamin ta kai kofar ta fadi kasa ta kwala wani irin ihu sai numfashinta sama-sama. Jin ihunta yasa kowa ya taso da gudu suka nufo dakinta. *Allah ka ba mu ikon yin domin ka. Bari domin ka, k'i domin ka, so domin ka. Wanda duk be ji tsoron hakkin wani ba kuma be ji tsoron Allah ba Wallahi ya yi aikin banza. Allah ka raba mu da aikin dana sani, ka doramu a daidai alfarmar Annabi Muhammadu Rasulullah Sallalahu Alaihi Wassalam* 6k Words 😲 Kun sha karatu har kun gaji. *Littafina na kudi ne, biya duniya ko kuma inda mutum be da su indai rubutun nan hakkina ne. *Z A K I -it's not free, pay 300 to 0314795884 Abubakar Gt bank, then send the evidence via 08036126660* *Ina mata son rage kiba? Ina mazan da kiba ta hana su sukuni? Ina masu jikin yai kyau kamar na yarinya? Ina masu fama da kujera ko wani ta bo a fuska? Ina masu fama da hawan jini? Masu diabetic? Ag cera an gwada yayi an tantance ingancin babu shakku ko kadan. AG cera ya zo domin ya temaki garkuwan jiki da kuma lafiyar jiki. Sinadari ne wanda ze magance matsaloli da dama wadanda suke hana garkuwan jiki aiki yadda ya kamata ko kuma yake rusa garkuwan jikin ita kanta.* *Cututtukan zamani daban daban sun sa mutane gaba kuma magance su yana da wahala; irin ciwon Sugar, hawan jini, ciwon sanyin kashi, ciwon gabobi da sauran su. Haka ma cutukka irin wadanda suka shafi fatar jikin wadanda sun hada da kyasfi, pimples, takurewar fata, rakainuwar fata da kuma haske da kyallin fata duka ana shan AG cera kuma yana temakawa wajen magance illolin nan. Mutane masu fama da rashin karfin jiki wajen kwanciya da iyali da kuma mata masu fama da yawan ciwon mara lokacin al'ada ta karshen wata suma baa bar su a baya ba. A takaice dai AG Cera yana temakawa wajen magance cuttukka daban daban wadan ke damun mutum. Domin karin bayani ku tuntuni mu a wannan number +60167474649 ko kuma ku ziyarci shafin mu http://agnutritioninternational.com.* A lokacin da ya shiga wanka ni kuma sai na dauko tsintsiya na share dakin lokacin da na fito da sharar a falo sai gashi ya fito daure da tawul a jikina ya tsaya bakin kofar dakin yana kallona. Nima kallonsa nai ganin be ce komai ba yasa na ce. “Har ka gama wanka ne?” Be ce min komai ba sai ma kara hade fuska da yai, tunani na tsaya na san dai kamin ya shiga wanka ban masa wani abun ba, kusan ma tun da aka daura mana aure Aliyu be taba yin fushi da ni ba sai amman yadda na ga ya hade rai na san ba lafiya ba. Kallon jikina nai duk da nasan ba a jikina ba ne matsalar domin ni kadai ce a falon ba tare da kowa ba balle har ya ce wani ya ganni babu Hijab. “Wani abun nai ba daidai ba?” Na tambaya ina turo baki kamar nima din wani abun akai min. “Yanzu ba dan neman magana ba, miye na wani daukar tsintsiya ki yi shara daga nan sai kice mopping za ki yi ki yi wankewanke da wasu abubuwa ko? Na san halinki ai, kuma can da da kike ke kadai ba ki yi ba sai yanzu da kuka zama ku biyu?” “Ina yi ai ko lokacin?” “A gidan Momy ko? Tun da aka miki aure kin taba shara? Sai yanzu za ki tsiro saboda neman magana kuma idan na ce ki daina ki fara min gardama?” Na jefar da tsintsiyar. “Na daina, naga gidan yayi datti ne kuma babu mai sharewa” “Da muka dawo haka kika ganshi? Kin san lokacin da ake shigowa a share ko a goge ne?” Na rausayarda kai. “Wuce ki yi wanka za mu je mu yi ma Mama barka da tashi, kuma za mu koma asibitin gurin likitan” “Mi zai min?” “Zan siyo magani a can kuma ina bukatar ganinsa dan ya fada miki irin abubuwan da zaki rika ci da yi da kunnenki kiji domin ni kin raina ni idan na ce ki daina sai kokarin yi za ki yi” “Aa ban fa raina ka ba” “Zamu gani” Ya fada yana jam kumatuna ba tare da ya mim murmushi ba, a dole na koma ciki nai wanka na shirya kamar yadda ya bukata, a tare muka fito da shi yana kallon yadda yake kallon tafiyata wata kila so yake yai sauri ko na taka ba daidai ba yace da gangan na ke yi saboda ina da ciki. Shi ya bude min motar na shiga sannan shi ma ya shiga ya zauna, sai ya kai hannunsa a bakinsa yana karanta abunda ban san ko minene ba sannan ya saka dayan hannunsa ya daga Hijab dina ya bude rigar zanen da ke jikina ya shafa min addu'ar a ciki. Sannan yai ma motar key daman tuni mai gadin ya bude mana gate, a hankali ya fara tukin har muka fito daga cikin gidan. Na yi zaton gidan za mu fara zuwa sannan mu wuce asibitin sai ya fara zuwa asibitin sai dai ba wacan ba ce domin wannan katuwa ce sosai ga ma'aikata ta ko'ina gwanin ban sha'awa. File aka fara bude min sannan ya sake tambaya ko ina jin sani abun bayan abunda na fada mishi jiya. “Bana jin komai” A nan ya sake rubuta wani abun a farar takadar ya mikawa Aliyu. “Ka kara mata da wannan, wannan kuma results dinku ne na jiya congratulations” Aliyu yayi murmushi yana kallona, kunya ce ta rufe ni nai kasa da kaina ina watsa da yan yatsuna cikin Hijab. “Doc ka fada mata abunda ya kamata tai da wanda be kamata ba da abubuwan da zata ci” Aliyu ne ya bukata da kansa, a take likita ya fara lissafa min irin abubuwan da zan rika ci da kuma aikin da zan yi wanda ba mai wahalarwa ba. “Aa no doctor ni fa ko bokitin ruwa ba zata dauka ba, balle wani shara da wanke wanke” “No ai aikin yana da kyau amman kar ayi na kashe kai” “Ko na raya kai ba za ayi ba, balle na kashe kai, ina ciki fa aka ce Alhaji” Aliyu ya fada yana nanatawa, shi kuwa likitan sai dariya yake, ni dai gaba daya kunya ta gama kamani har bana iya daga kaina. “Ta so muje” Tashi nai ina tafiyar cike da kunya shi kan tuni ya kai kofa har ya bude min kofa yana jira na fito, sai na fita sannan ya fito, ba ko kunya ya kama hannuna zuwa gurin motarsa da kansa ya bude min sai da na shiga na zauna sannan ya rufe ya zagoyo gefensa ya zauna, tukin mota yake amman gaba daya hankalinsa da tunaninsa na kaina, minti biyu uku sai ya kalli inda na ke. “Kina son wani abu? Kina jin wani abu?” Yayi min irin wannan tambayar ta kai sau takwas kamin mu isa family house na su, a harabar gidan ya faka motarsa har na kai hannu zan bude sai ya danna dan wani abu dake gefen motarsa motar ta rufe, kallonsa nai sai ya fara min magana a natse. “Kin dai ga cikin mutane ne, bana son ki je ki ci wani abun da zai lalata miki ciki ko ki ci da yawa, kuma ki ci yaji ko ki zauna da yunwa, da ama ace Mama ce kadai ko Ammy zan iya yi miki magana a ganbansu amman Mama (Nana) ba zan iya miki magana a gabanta ba, pls ki kula da kanki” “Tau” “I love you” Ya fada sannan ya cire abun ni kuma na bude motar na fita ta nufi bangaren Ammy, sai na ji ya kira ni. “Babyna, za mu fara zuwa mu gaishe da Mama” Juyowa nai na karaso inda yake tsaye ba tare da na ce masa komai ba, a tare muka jera muna tafiya zuwa part din Mama Fulani, yana ta kallon yanayin tafiya kamar mai kirga yadda na ke takawan. A falo muka samu Mama Fulani zaune kanta sanye da hular wanka hannunta kuma rike da brush an zuba masa mai daurin kirji ne a jikinta sai kuma wani karamin tawul da ta rufa a saman jikinta, Rukaiyah ya mata kafafuwanta. Zaunawa yai kusa da ita, ni kuma na zauna a dayar kujerar sai kallona take kamar bata taba ganina ba, gaba daya ta wani yi sakuku kamar ba ita ba, ni ban taba ganinta a cikin yanayin tausayi ba sai a yau. “Mama yanzu kika tashi?” “Eh Aliyu” Ta amsa tana aje numfashi. “Na'am, amman Mama ba ki jindadi ko?” Ya tambaya cikin yanayin da ke nuna tsantsar kulawarsa a gareta. “Muhseen ya duba ni ai, kuma yanzu idan nai wanka na karya zan sha maganai” “Mama ina kwana” Na fada ina dan risino kaina alamar girmamawa, sai ta kalleni kawai ta kasa amsawa kamar mai jin nauyi ko kunya, mikewa tai tsaye ba tare da ta amsa min ba ta nufi hanyar dakinta sai da tai rabin stairs sannan ta juyo ta kalleni sai kuma ta dauke kai ta shige dakin. “Ku baku iya gaisuwa ba ne?” Maganar Aliyu ta saka na maida duba a gurin Maryam da ke gyaran cucumber da kuma Rukaiyah wacce ta gama matsawa Mama Fulani kafafuwanta. “Ina kwana ya Aliyu?” Har sauri suke gurin gaishe shi suna hada baki. “Ba ni ba ita, matata ce yadda kuka respecting dina haka ita ma za ku mata” Ya fada babu alamar wasa a tare da shi, a tsakanin Rukaya da Maryam ban san wa yafi wani nauyin baki gurin gaishe ni ba, ni kan wani irin kunya da girma ne ya rufe ni a lokacin ba dan na san sai ya cilasta ni amsawa ba da ba zan amsa ba, sosai na ji daraja ta ta dagu, ba kuma dan sun san wacece ni a yanzu ba, sai dan auren dan'uwansu da ke wanda ya zama dole su girmamani ko da kuwa sun haife ni. “Ta so muje bangaren Ammy mu gaishe su” Ba musu na mike tsaye, ina gaba yana bayana har muka fito daga part din Mama Fulani muka nufi bangaren Ammy. “Ba dan Mama tana jin kunyarki da nauyinki ba da yanzu ta rumgume ki tana nuna miki jindadinta da farincikinta aka my samun cikinki” Ban ce masa komai ba, muka cigaba da tafiya, fuskarsa ba yabo ba fallasa muka nufo bangaren Ammy sai dai muna shiga falon ganin Muhseen zaune yasa ya dan canja fuska kamar be ji dadiba, ni kan har na yi farat zan fara masa magana sai na tuna cewar ina da aure a yanzu kuma ina tare da Aliyu. A saman kujera yake zaune Kamar yadda Ammy da Nana ma suke zaune a saman kujera, tun da nai sallama ya dago kansa ya kalleni sai ya maida idonsa gurin wayar be sake dagowa ba, har na zauna ina gaisawa da Ammy da Nana, Aliyu ma ya gaisa da ita, sai Muhseen ya mike tsaye ya face daga falon idonsa akan wayarsa ni kuma na bi shi da ido ina juyowa Aliyu ya watsa min harara a cikin sigar da babu wanda zai gani ya fahimta sai ni da akai wa. Mikewa yai ya fice daga bangaren Ammy ya bar a nan, ni kuwa na tashi na koma kusa da Nana na zauna a kasa na dora kaina saman kafafuwanta, sai ta fara shafa kaina tana murmushi. ALIYU POV. Sam be jidadin ganin Muhseen ba ba kuma dan komai ba sai dan yana tare da Ataa, idan ya tuna cewar Muhseen ya taba son Ataa abun tana taba shi kuma yana jin babu dadi, duk kuwa da kasancewar ya aureta amman wannan kishin yana nan cikin ransa. Ko da ya shigo bangaren Mama Fulani yayi zaton zai samu Muhseen a falo ko dakin Mama Fulani amman sai ya samu akasin haka, domin kuwa Mama Fulani ce kadai a dakin zaune rike da brush din dazun tana kallon wani gurin kamar mai tunanin domin shigowarsa kadai har da zabura tai. “Mama har yanzu laifina kike gani?” Bata ce masa komai ba sai lasa lips dinta da tai cikin yanayin damuwa. “Wallahi Mama Nasir ne ya kawo min wannan shawarar amman ba wai dan wata manufar nai ba” “Ina maka murna Aliyu wannan babban abun farinciki ne da jindadi, ba zan iya fada maka ko misalta maka yadda na ke ji a yanzu ba, sai dai abun bakinciki na zan iya nuna ba” “Saboda mi Mama” “Kai ma ai ka sani Aliyu duk wani abun da zan musu a yanzu ko na nuna farincikina ba yarda za su yi da ni ba, kuma har abada Ataa ba xata daina ganin cewar bana sonta balle kuma abunda yake cikinta. Aliyu kunyar kaina na ke ji, kunyar kaina na ke ji sosai” Ta fada idonta cike ta kwalla har ya fara sauko mata, murmushi Aliyu yai yana kokarin nuna mata shi be ga wani abun damuwa ba. “A rashin sani kika aikata Mama, kuma ni danki ne, Ayusher ta sani dole ki so abunda yake cikina tunda har kina so na, na fada mata bani da kamar ke da Momy a duniyar nan, ni yanzu abunda na ke so ma idan kin yi wamka kin shirya kije ki roka min Mamanta ta bar min matata ni ba sai ta je d ita can nijar ba” “Nijar za su tafi?” Ta tambaya tana share hawayenta. “Eh ta fada min tun shekaranjiya cewar Mamanta tace za su tafi ta ga dangi tare da Sarkin Agadaz za su tafi idan zai wuce, da na yi nijar bin ta muje tare, yanzu kuma na canja sha'awara gaskiya idan tai tafiya mai nisa da wani ganin dangi jagalgala cikin za ayi, kara dai tai hakuri sai idan ya girma sai mu tafi tare ko kuma idan ta haihu” “Gaskiya ni ma ban bada goyon bayan ta tafi yanzu ba, taya zata fara yawo da karamin ciki ma?” “That's why I love you Mama, kina da mugun fahimta, yanzu dai ki yi wanka sai ki je ki yi magana da Mamanta ki roka min ita” “Aa ba zan iya ba” “Zaki iya” “No-no Aliyu i can't ai da kunya nai maganar a yanzu ma, duk abunda zan yi kar suke kallona, jiya mahaifiyarta ta kasa sakewa da ni, itam Ataa ba so zata tai b Wallahi balle har tai tunanin abun kwarai zan mata” “Mama pls for me? Ai za ki iya min komai ko?” Ta gyada kai cikin damuwa. “To pls ki yi magana da ita as my mother kuma saboda grandchild dinki ba wai as abunda kika aikata cikin rashin sani ba” Yawun bakinta ta hadeye ta tashi ta nufi bandaki cikin yanayin damuwa. *Manage pls* “Ina ganin zai fi kyau idan ka hakuri ka bi matarka Aliyu, ko kuma ka kira Momy ko Ammy ka rikesu su yi ma mahaifiyarta magana idan zata yarda ta barta na wani lokacin idan cikin yayi kwari” Tana zaune bakin gado take fadin wannan maganar bayan ta fito daga wanka, Aliyu ya dago kansa daga kan wayarsa ya kalleta. “Ko na bita hankali ba zai kanwata ba Wallahi, kuma kin san ba ni wanda zau shige min gaba yai min ruwa da tsaki a wannan lamarin sai ke” “Ba zan iya ba Aliyu, Wallahi ina tsananin jin kunyar kaina balle kuma na hada ido da Ataa ko mahaifiyarta, da ace komai be faru ba da yanzu ba haka ba” “Amman Mama” “Aliyu ba zan iya ba, dan Allah ka je ka samu Ammy ko Abbahku kai masa wannan maganar” Ta amsa masa kai tsaye da dukannin gasjiyarta, taya ma zata iya zuwa ta ce zata roki abar Ataa saboda cikinta? Yarinyar da ta gama wulakantawa ta aybanta. Ai wannan ya zama rashin kunya ma. Aliyu be sake cewa komai ba, ya mike tsaye ya fice, har ga Allah baya son tafiyar Ataa a garin nan yanzu ya san duk yadda zai bata kulawa a nan dole a can sai ya daga mata kafa wani abun ma ba a gaban idonsa za tai ba, gashi tafiya ce ba nan kusa ba, waya sani ma ko ace sai taga kowa da kowa tukuna za su dawo? Ba wai baya son haduwarta da danginta ba ne, shi yadda za a jigilgila cikin ne baya so. Yana son cilasta Mama Fulani tai ma Nana magana ne saboda bakinta da na Nana ya hadu a wani gurin na nunawa Ataa kulawa, ko da ba zata yarda ba akalla yasan Nana zata san cewa Mama Fulani ta damu a yanzu, and hakan da za tai a yanzu matakine na murje ido ta nuna komai ba komai ba ne yadda za a zama abu daya, amman ya saka samun hakan daga gareta, ya sani abunda Mama Fulani ta aikata ba daidai ba ne, shi kanshi baya ganin laifinta ko ganin kuskurenta har sai yanzu da yake kokarin gyara na shi kuskuren. Cikin mota ya koma ya zauna ya kira wayar Nasir tana yin ringing  yai picking kamar mai jiran kiran. “Babban Baby gani a hanyar gidanka fa da Madam” “Gurin me?” “Zata zo ta ga Ataa ne kasan ba su taba haduwa ba, and tana son taya ta murna samun ciki” Yar dariya Aliyu yai shi kanshi Nasir sai da yai dariya sannan aliyu ya dora da. “Bana gida ni da ita muna nan gurin Mama, Nasir ina son magana da kai” “Ayyah bari na sauke ta gidansu yayarta zai na same ka a can” “Alright” Aliyu ya kashe wayar yana ta kallon garden gidan da ke facing din inda motarsa take fake. Fita yai daga motar ya nufi bangaren Ammy sai kuma ya samu kansa ya kasa shiga ciki sosai yake jin kunyar Nana shi kanshi har Mamakin abun yake, domin ko iyayen Rahma yana sakewa da su da su ne kai tsaye zai iya nuna musu baya son matarsa tai nisa da shi balle kuma ace tana da ciki abunda yake kauna. Har ya ciro wayarsa ya kira Ataa sai ya tuna da be saka mata line a ciki ba, a take ya aikama Nasir text, sannan ya juyo zai dawo part din Mama Fulani kuma sai ya hango Muhseen ya shiga can sai kawai ya nufi gate yana ta sake sake a ransa, he can't face Nana kai tsaye ya fada mata haka and idan Mama Fulani ba zata iya zuwa tai magana da Nana ba ba zai iya rokon Ammy ba, domin a ganinsa idan har Nana da Mama Fulani ba su samu fahimtar juna ba shi kan shi yana cikin matsala. Bakin gate din ya fito ya tsaya yana danna wayarsa, number Rahma ya kira tai ringing har ta katse ba a daga ba, ya sake kira ba a daga ba ya san wannan baya rasa nasaba da fushin da take da shi, sai kawai ya aika mata da sako. Jin motsin mutum da yai bayansa, zuciyarsa ta raya masa Ataa dan yasan ita kadai zata masa haka duk duniya sai kawai ya saka hannunsa ya rikota ta baya ya juyo da ita, sai ta saka dariya. “Mi ya kawo ki nan?” “Naga lokacin da ka zo gurin Ammy ai sai kuma ka  koma” Kallonta yai sai kuma ya kalli gate din gidansu Kamal a take zuciyarsa ta raya masa cewar Kamal zai iya fitowa ya ganta, and abunda ya fi tsana a yanzu wani wanda ya tana son Ataa ya ganta ko, a duk lokacin daya tuna cewar Ataa ta furta masa cewar tana son Kamal sai ya ji ba dadi. “Koma ciki nima Nasir na ke jira” “To mu jira shi tare miyasa ka fasa shigowa ciki?” “Kunyar Mama na ke ji, ke ma ki je ciki Mama Fulani na son magana da ke” “Ni?” “Yes shiga gida mana” Ya fada mata calmly yana kallon cikin kwayar idonta, wani irin kaunarta yake ji cikin ransa. “I Love you” Ya fada mata a hankali, sannan kama hannunta ya rika sai kuma ya saki ya tura hanninsa ya bude mota kofar gate din, har ta juya ta shiga Muhseen ya fado masa a rai sai yai saurin bin bayanta. “Babyna karki je yanzu zo ku yi magana da ke a mota” Gaba yai zuwa gurin motar ta biyo, jinginawa tai jikin motar shi kuma ya tsaya daga gabanta yana kallonta from head to toe wani dadi yake ji wai cikinta ne a jikinsa. “Babyna gobe Mama za ta tafi ko?” “Eh amman da ni zata tafi ai” “Ni kuma ki yi yaya da ni?” “Sai na je da kai” “Ba a zuwa da babba yawo” “Sai ka zauna har mu dawo” “Za ki iya tafiya ki bar nan?” Sai tai shiru, tai kasa da kanta. “Babyna kin ga kina da ciki? Kuma cikin nan sabo maganin ma yanzu za ki fara sha idan na siyo, kuma kin ga ciki yana son kulawa musamman sabo, bana son ki yi tafiyar nan dan Allah” Ta lake kafada tana turo baki. “Ni gaskiya ina son na ga yan'uwan Mamana kuma su ma za su so ganina ai” “Ciki be so jigila ai da yawan zirga zirga idan yana yaro, ba za ki iya kula da shi yadda ya kamata ba” “Ai sai muje tare idan ba ka yarda da ni ba” “Daman ai ya kamata na je saboda na san iyalinki kuma su ma su san ni amman wannan cikin ne ya saka na canja tunani” “Ni gaskiya ina son na je, kuma Nana ba zata ji dadi ba idan ban je ba” “Ba na ce ki daina ce mata haka ba?” “To Mama” “Idan na ce zan biku yanzu ai ya zama rashin kunya, kuma idan muka je can ba guri daya za mu tsaya ba, kin ga dole kije nan kije nan ana nuna miki dangi, Wallahi Ataa cikin nan a jikiki kawai yake amman jinshi na ke a cikin cikina, ni da akwai yadda za ayi da an maida min shi ke kije ki yi ta abunda kike so, ba ki san yadda na ke jin cikin nan ba ne” Ya fada cikin yanayin damuwa, domin har ga Alla shi gani yake idan tai wata wahalar zai iya rasa cikinsa. Dariya tai masa sosai kamin ta ce wani abu suka ji horn a bakin gate din gidan, mai gadin ya bude wanda hakan ya bawa Nasir shigowa cikin gidan da motarsa. Ataa ta maida dubanta gurin motarsa har ya faka motarsa kusa da Ta Aliyu ya bude ya fito, Aliyu can't take his eyes on Ataa sai da Nasir ya fito daga motar sannan ya juyo yana kallonsa. “Madam congratulations” Aliyu ya kalli Ataa wacce tai kasa da kanta tana jin kunya shi kuma yai murmushi yana saka hannunsa aljihu. “Ina wuni” Ta gaisheshi cike da kunya. “Lafiya kalau ya jikin na ki” “Na ji sauki” ta juya da sauri ta nufi bangaren Mama Fulani a lokacin ne Muhseen ya fito daga part din ita kuma ta shiga. Aliyu ya bude motarsa ya dauko takadar maganin ya mikawa Nasir. “Zaka saka a binciko mana wannan, na so na siya asibiti kuma ban samu dama ba” “Ka ce kana son mu tattauna” Nasir ya fada bayan ya karbi takadar. “Yeah zancen tafiyar nan ne Nasir bana son zuwanta, kuma na rasa yadda zan shawo kan abun, ga shi kuma Mama Fulani ta ki yarda tai magana da Mahaifiyarta, and you know Momy ba za tai ba” “To kai miye damuwarka da zuwanta? Ba abun farinciki ka ne ba sai ka je ka ga danginta su ma kuma su ganta” “Na sani ai, Nasir cikin anan kasan karami ne” “Aliyu ba akanka aka fara ciki ba, wannan ba ma reason ba ne kuma ka san ba ka isa ka samu Mahaifiyarta da wannan maganar ba, dama daya ce da kai ka bita ku tafi ka ga danginta idan ma da kai ba za a barta ta dade ba, sai ku dawo abun ku sai kuma ta haihu, amman idan za ka iya convince dinta da yarda ta zauna then fine” “Ai ba zata yarda ba ne” “Kai ma ai kasan yadda take dauki ganin yan'uwanta kamar yadda kake daukin cikinta” Aliyu yai murmushi domin shi kadai ya san abunda yake ji akan cikin nan nata. “Gobe fa za ayi tafiyar” “Shirinka ai ba shi da wahala sai ka shirya kawai ka bi su” “Babba da ni” “To ya ka iya kauna ce sila” Dariya Nasir yai yayinda Aliyu kuma yai murmushinsa da ya saba. ***      ***      *** After fitar Aliyu Mama Fulani ta dauki wayarta ta kira Momy ta labarta mata abunda ya faru tana rokon ta yi ma Nana magana saboda ta fi ganin kimarta sama da ita, kuma tana ganin kamar ran Aliyu ya bace saboda ta ce ba zatai maganar ba. “Wannan aikin ai na ki ne Fulani, ke da danki akwai wanda ya isa ya shiga tsakaninku?” “Da dai ace duka sannan be faru ba da zan iya yin komai amman yanzu bana da wannan yancin” “Ki manta da abunda ya faru, dukan abunda ya faru kin aikata ne a cikin rashin sani da kuma rashin tunani, daga d'an ki har ke kun yi wa talaka da talauci wata gurguwar fahimta ne, ba ku ganin kimar wanda ba shi da shi matukar mutum talaka ne ba shi kima ba shi da yanci a gurinku, shiyasa bana son munana kiyayyah ko tsananta soyayyah wata rana wanda kake ki ne zai dawo masoyinka wanda kake so kuma ya zama makiyinka, tun daga lokacin da Nasir ya labarta min zancen samun cikin na ga ba ki kirani ba na san ba ki cikin jindadi, ba kuma na samun cikin ba sai na kunyar abunda kika aikata, a yau duk wata naira da izzar dukiya da kike takama da ita Fulani Ataa ta damata ta shanye tun da kuwa Kakanta ne mai wannan arzikin, kuma na jidadin hakan wata kila da ba ta haka abun ya zo ba da har yanzu ba ki gane cewa akan kuskure kike ba, wata kila da har gobe ba zaki yi nadama ba balle a ranki kiji ko cewar kin aikata wani abu da ba daidai ba, na tabbatar da Ataa ta yi arziki ne ta hanyar d'anki da har jibi sai kin mata gori kuma kina ta kallinta kallonta da wannan tambarin na talauci wanda ba ita tai ma kanta shi ba, amman da Allah ya so nuna miki isarka da ikonta sai ya kawo wanda daga ke har Rahma za ku zauna a karkashin inuwarsa kuma ku wayi gari jininsa kuke wulakantawa” Tun da Momy take maganar Mama Fulani take hawaye ko wani harafi da za a hade da dan'uwansa ya bada ma'ana sai da ya taba zuciyar Mama Fulani. “Abunda ya faru ya riga ya faru, ki manta da komai ki maida komai ba komai ba, ki murje ido ki nunawa Ataa kulawa da kauna, domin su ne kadai abunda take bukata a yanzu, har yanzu akwai abubuwan da Ataa ta rasa, ilmi, iya mu'alama da mutane, zamantakewar rayuwa, girki da kuma zaman aure, Ataa yarinya ce da har yanzu bata wayancin wasu abubuwan ba, za ki iya maye mata gurbinsu a yanzu cikin hikima za ki nuna mata soyayya da nadamar abunda kikai, ko ba yanzu na sani dole wata rana za ki so Ataa ko ki zauna da ita dan dole tun da danki take aure, Fulani wannan ya iashe ki izna talaka ba abun wulakantawa ba ne, ko da ko ba ta irin sigar da Ataa ta zo miki ba, ba ki san inda wani talakan zai taima ke ki ba, ita rayuwar duniya makaranta ce dukiya da talauci kuma dukansu jarabawa ne ya kamata ki gane wannan” Mama Fulani ta gyada kai kamar Momy na gabanta. Sannan ta saka hannunta ta share hawayenta . “Na gane, amman har yanzu ina jin tsoro kuma ina kunya sosai” “Wallahi ki gode Allah daya nuna miki haka tuna a yanzu ba sai da kika fada wata mummunar rayuwar ba, kuma ya saka miki saduda a take, daman can ban ga wani abun dagawa a dukiyar da zaka mutu ka barta ba, da arzikin da ba zai iya hana ka ciwo ko tsofa ba balle kuma mutuwa, yanzu dai abunda ya fi ki tashi da kan ki kije ki yi magana da mahaifiyarta ki yi kamar komai ba faru ba, ni kaina bana ra'ayin zuwanta gidan a yanzu, domin na san halin dan ki ba komai zai gani ya kyale ba sai yai ta nuna rashin kunya a gidan sarauta kuma ba a haka, kara dai sai cikin ya yi kwari” “Allah Momy ba zan iya ba, abun da kunya sosai” Daga dayan bangaren Momy ta yi dariya jin abunda Mama Fulani take fada wai da kunya, yau Mama Fulani ce take cewa tana jin kunyar yin wani ba wacce ke bugun gaba tana ganin ita tana da kudi kowa zata iya tinkara ta fada masa magana kai tsaye, kuma jin kunyar ma ta Ataa yarinyar da ta gama wulakantawa tana nuna mata ita din ba kowa ba ce. “Na fada miki idan kika ce za ki dauki zancen kunya ki saka a ranki za ki yi ta cutar da kanki da d'anki ne kawai, ki kasa sama masa abunda yake so ke ma kuma ki kasawa bawa kanki, ni dai ina farinciki da yadda na ji halin nan ya sauko Wallahi, na dade ina jiran zuwa wannan ranar amman ban samu ba sai yau na dade ina nuna mu ku abunda kuke kuskure ne amman kuka kasa fahimta, sai da Ataa ta zo, lallai Ataa ta zama alheri a familyn mu” Ajiyar zuciya Mama Fulani ta sauke a hankali sannan ta sake share hawayen da suka zo mata. “Ina murna da samun cikin nan abunda muka dade muna nema, ashe Allah ya rubuto sai ta bangarenta za a samu, Allah ya inganta ya bata lafiya kula da shi” “Ameen, yanzu kulawarta a hannunki take tunda kin san a nan za su zauna kusa da ke” Mama Fulani ta yi shiru tana kallon Muhseen wanda ya shigo hannunsa rike da wasu magani har kala hudu. “Na gode Sai kin sake ji na” Mama Fulani ta fada sannan ta katse wayar tana cigaba da kallon Muhseen wanda fuskarsa ke cike da walwala. “Mama ki sha wannan maganin yanzu” “Na dazun ma ban sha na fa” “Miyasa da kin sha ai sai ki sha wannan yanzu kawai, amman ki bar wacan ki sha wannan” “Duka? Na ji zazzabin ya sauka ma da nai wanka fa” Kusa da ita ya zauna yana murmushi. “Mama ki sha kawai likita kika haifa fa, sai dai anjima zai iya dawo miki tunda tunanin yana nan cikin ranki” “Tunanin me?” Ta tambaya tana nuna kamar babu abunda ya dame ta. “Na abunda ya faru mana Mama, kina ta jin kunyar Ataa ko?” Ta yi shiru bata ce komai ba. “Wallahi tun daga lokacin da kika fada min labarin nan, sai Ataa da mahaifiyarta suka kara burge ni, yanzu irin yarinyar da ake wulakantawa kamar haka ace ta san tana da family irin wannan amman ta yarda ta zauna a haka ta jure wulakanci da cin mutunci, kin san da wata ce tun daga lokacin da suka fara shiga gararin rayuwa za su fara neman yan'uwnasu ko da yankasu za ayi a ci namam su? Wani abun farinciki faruwar wannan abun ya saka a take jiki ya yi sanyi, kin zubar da makaman yakinki ga shi har kina jin ba dadi a abunda kika aikata, dubi Aliyu dazun davya shigo tare da ita part din Ammy abun har mamaki yake ba ni mai tsanar talaka ya koma son ta ko kunya be ji ba, ke ma kuma kina jin kunyar talaka kamar ba ku ba gaba daya, tun yaushe na ke son rayuwar ku ta canja Mama? Tun yaushe na ke nuna muku cewar talaka ba abun wulakatawa ba ne, amman kuka kasa ganewa ke da d'an lelen danki har kuna ganin kamar ni da Momy ba mu waye ba ne, lallai Ataa yar baiwa ce ita ta canja muku komai cikin kannen lokaci, ni kaina ina cikin farinciki a yanzu domin na samu wace ta fita, kuma raina yake so fiye da ita but the most funniest part Aliyu kishina yake har yanzu, ni kaina dunno why na ji kamar na tsani Ataa, but seriously tana burgeni akan wannan abun daya faru” Mama Fulani ta mike tsaye ta nufi bandakinta ta dauka fanfon ciki ta kunna ta sha maganin sannan ya fito tana fadin. “Yana ta damuna wai na je na yi magana da mahaifiyar Ataa akan tafiyar da za su yi kar su je da ita, ko kuwa ba ni da wannan damar a yanzu” “Saboda me? Ataa fa dole ta girmamaki indai har tana ganin kimar mijinta, ke fa uwa ce a gurin Aliyu” “Na sani amman ba yanzu ba” “Yeah komai da sannu zai wuce kamar ba ayi ba Mama In-Sha-Allah” Ya fada yana mikewa tsaye. “Ya maganar kayanka? Idan ka shirya komai sai na yi ma Abbah ku magana” “Ba yanzu ba Mama sai hankalinki ya kwanta, na fi son ayi komai kina cikin farinciki” Ta gyada masa kai shi kuma yai murmushi ya fice. ATAA POV. Da tunanin abunda Mama Fulani zata fada min na shiga bangarenta, Aliyu ya fada min cewar tana son magana da ni amman akan me? A hankali na tura kofar falon na shiga babu kowa a ciki sai sanyin ac, ni kuma na zauna a saman sofa ban yi kaudi ko tunanin hawa sama inda take ba na zauna zaman jiranta har ta zuwa lokacin da za ta sauko. Na kusan awa daya a zaune bata fito ba kuma wani be shigo ba, har na mike tsaye da zimmar fita sai na ji motsin saukowata hakan yasa na koma na zauna na daga kaina ina kallon yadda take takowa har ta sauko kasa, wani gefe gafe take da ido kamar ba ta ganni ba ko kuma bata son kallona. “Mama Fulani Aliyu ya ce kina son magana da ni” Shiru tai na wani lokaci kamin ta amsa min ba tare da ta kalleni ba. “A a, wata kila dai be gane ba ne” “Tau” Sai da na mike tsaye sannan ta kalli inda na ke sai kuma ta dauke kai, ni kuma nai ficewata ba tare da na sake ce mata komai ba, a harabar gidan na ga karin motoci har biyu ba zan iya shaidar motar waye da waye a wajen ba, amman dai na san bayan motocin da suke fake a cikin gidan sai kuma ta Aliyu da Nasir yanzu kuma wasu ne har biyu irin mayan motocin nan na alfarma. Littafin nan na kudi ne, idan kin ganshi waje na sata ne. Bangaren Ammy na nufa kai tsaye daman na fi zargin bakin ko can suka zo tunda ban ga kowa ya shigo gurin Mama Fulani ba. A lokacin da na shiga falon Ammy sai na tarar babu kowa a ciki, kamar yadda na barta dazun zaune da Mama wato Nana da Aliyu ya lakanta min sunan Mama a saman nata na Nana da na ke kiranta da shi. Zaunawa nai na maida hankalina gurin tv dake kunne. Ba jimawa Ammy ta fito daga bandakin da ke falon tana kallona ta saki murmushi. “Yanzu nan kuwa Hajiya ta fita” “Ina suka je?” “Suna bangaren Abbah, ya zo da wasu baki shine ya kirata” “Ok” Na fada ina ta tunanin ko su waye ne. Sai ga Aliyu ya shigo falon rike da line a hannunsa. “Ina wayarki” “Gata nan” Na ciro ta daga koguna na mika masa ni na ma manta da wayar sai yanzu da yai maganar, tun a lokacin da na nunawa Mama ita na biyo ta ajikin gudun kar na manta da ita ban tuna ba sai yanzu. “Ina kika saka ta?” Ya tambaya yana min wani kallo kamar na mamaki ba tare da ya karbi wayar ba, kamar dai ya manta cewar ba daga ni sai shi ne a falon ba Ammy ma tana nan. “Aliyu dan ta saka waya a jiki sai ya zama laifi?” Cewar Ammy tana murmushi shi ma murmushin yai sai dai ba sosai ya karbi wayar ya bude yana saka Sim wani dadi ne ya lullube ni ganin layi ne zai saka min hakan na nufi zan iya kira kuma a kirani. “Ta so muje” Tashi nai na bi bayansa yana gaba ina biye har muka isa bangaren Abbah, tun kamin mu shiga na fara jiyo muryar wasu na watso turanci kamar turawa sai hayani suke a falon har da muryar mace. Dan tsayawa nai na janyo rigar Aliyu. “Su wanene?” Na tambaya kadan kadan kar su ji. “Idon ki za su cire” Ya fada min babu alamar wasa a fuskarsa kamar da gaske haka din ne. Sannan ya tura kofar falon ya shiga, ni ma na shiga da dan tsoro. Dukansu suna sanye da suit mata biyu maza hudu mace dayar tana sanye da karamin Hijab a wuyanta, dayar kuma kanta a sake ta saka jam gashi mazan biyu kuma suna rike da abun rubutu. “Ke ce Ataa?” Kabilar ta fada da hausa sai na gyada mata kai. Ina ta bin Aliyu duk inda yai har na zauna a inda ya zauna. “Bude ba ki za ki yi ki mana magana, daga sama aka turo mu nan” “Ni ce” “Miye sunanki na gaskiya?” “Aisha” “Ya kike da wannan?” “Mamana ce” “Ita ta haife ki?” “Eh” “Mamanki tana da wani rashin lafiya ne ko wani ciwo?” “Eh bata da koda daya” “Garin ya?” “Wani likita ne ya cire mata” “Ya akai ya kai cire mata kodar kuma ya akai kika tabbatar cewar bata da koda?” A take na fara zana musu yadda komai ya faru. Har suka fara tambayana kamaninsa na bayyana musu da kuma inda asibitinsa take. Namijin ya nuna min hoton group din mutane a guri daya ya ce na nuna masa shi sai na nuna fuskarsa. “Za mu mika wannan statement din aga kungiyar likitoci reahen jiyar sokoto, su fara na su bincike kamin ya iso zuwa nan, and After that za mu dauki ke mu kai ki asibiti a sake miki hoto domin tabbatarwa” Ta karasa tana kallon Nana. Sai ta gyada mata kai. Sannan ta juya sukai magana da sunan su sai kuma suka mana sallama suka fice tare da Abbah ni sai a lokacin ma na ke lura da Nasir ashe har da shi yana zaune a falo har ma dayan jikan Mai Martaba wanda suka zo da shi. Aliyu da Nasir suka bi bayan Abbah, aka bar mu ni da Mama murmushi na gani a fuskarta na san ba zai wuce na jindadi ba kamar yadda nima na na jidadin ganin cewar za a kwato mata hakkinta, na yi zaton maganar zata fara min sai na ji ta ce. “Mai Martaba ya ce mu shirya duk abunda ya kamata a yau, gobe da safe za mu wuce Lagos daga can za mu tafi gida” “Waya fada wa” “Yusuf ya fada min lokacin da suka shigo, kuma ina fatar kin fadawa mijinki” “Eh na fada masa amman yanzu zan kara masa maganar” “Ina jindadi sosai zan ki ga iyalina ni ma kuma zan sadu da su da kuma mahaifiyata bayan tsawon lokaci, na jidadi sosai, na jidadi marar misaltuwa kuma ina cikin jindadin” Ta fada ya yaren buzanci idon na cika da kwalla. RAHMA POV. A hankali numfashinta yake shiga jikinta, idonta kulle hancinta kuma manne da oxygen, ga wani katon tukuyar shakar numfashi da ke aje gefenta tare da wata nu'urar da ke taimaka mata tai numfashin, idonta a rufe suke amman hawaye masu zafi ne suke gangarowa daga cikin idonta da ke rufe zuwa gefen ko wane kuncin fuskarta. Mommynta tana zaune gefenta idonta ya sumbura sosai saboda kuka gaba daya ta fita daga hayyacinta kamar ita ce marar lafiyar ba Rahma ba. Samun koda yanzu abu ne mai wahala, domin sun saka nema har yanzu ba a dace ba, balle kuma yanzu da likitocin suka tabbatar musu da samun ta a dole matukar suna son yar su a raye cikin koshin lafiya. Ba zata iya kallon yarta ta mutu ba, bayan tsawon lokacin data dauka tana jinya kuma tana son Rahma a cikin yayanta fiye da kowa, matukar aka kwana biyu ba a samu ba zata yarda a cire nata daya a dasawa Rahma ko da ko ita zata rasa ranta ne ko kuma lafiyarta, ba zata iya kallon Rahma ta bar duniya ba saboda rashin abunda zata iya samar mata ba, tunaninta da bakincikin mutuwar Rahma idan har ta Allah ta kasance ta san ita ma ba zai barta ta rayu ba. Da wannan kara kawai ta bata kodarta daya idan har zai yi, ita kanta ta san abubuwa sun yi ma Rahma yawa a yanzu, samun cikin Ataa, barinta da Aliyu yai ya auri wata, ga Kuma bullowar wannan lamarin na kakanta Ataa wanda ya zama karkashin inuwarsa dukansu suke rayuwa, ta alfahari da bugun gaba ta kare. *Ina mata son rage kiba? Ina mazan da kiba ta hana su sukuni? Ina masu jikin yai kyau kamar na yarinya? Ina masu fama da kujera ko wani ta bo a fuska? Ina masu fama da hawan jini? Masu diabetic? Ag cera an gwada yayi an tantance ingancin babu shakku ko kadan. AG cera ya zo domin ya temaki garkuwan jiki da kuma lafiyar jiki. Sinadari ne wanda ze magance matsaloli da dama wadanda suke hana garkuwan jiki aiki yadda ya kamata ko kuma yake rusa garkuwan jikin ita kanta.* *Cututtukan zamani daban daban sun sa mutane gaba kuma magance su yana da wahala; irin ciwon Sugar, hawan jini, ciwon sanyin kashi, ciwon gabobi da sauran su. Haka ma cutukka irin wadanda suka shafi fatar jikin wadanda sun hada da kyasfi, pimples, takurewar fata, rakainuwar fata da kuma haske da kyallin fata duka ana shan AG cera kuma yana temakawa wajen magance illolin nan. Mutane masu fama da rashin karfin jiki wajen kwanciya da iyali da kuma mata masu fama da yawan ciwon mara lokacin al'ada ta karshen wata suma baa bar su a baya ba. A takaice dai AG Cera yana temakawa wajen magance cuttukka daban daban wadan ke damun mutum. Domin karin bayani ku tuntuni mu a wannan number +60167474649 ko kuma ku ziyarci shafin mu http://agnutritioninternational.com.* ******* 55 Ba mu koma gida ba sai dare, Nana ta yi ta nanata min lokacin da za mu tafi kamar yadda Mai Martaba ya fada mata, a hanya Aliyu ya tsaya ya siya mana ayaba kankana sannan muka isa gida. Sai ya ya faka motarsa sannan na saki hannunsa na bude motar kamin na fito har ya zagoyo gefen da na ke ya karasa bude min ganbun motar. A hankali na sauko ina takawa yana rike da hannuna dayan hannunsa kuma rike da ledar da muka siyo ayaba. “Mama ta ce nai tuna maka zancen tafiyar mu fa” Be ce min komai ba, har muka shiga falon sai ya zauna saman kujera ya janyo hannun na zauna saman jikinsa ya rumgume. “Na sani ai, tare za mu tafi” “Da gaske?” Na fada cike da jindadi ina wara ido sai ya gyada min kai, rumgume shi nai na lafe a jikinsa kamar wata kyanwa yana shafa bayana a hankali. Mun dade a haka kamin mu koma daki, duk wani abu daya san zamu bukace shi a cikin daren ya hada mana shi, jaka daya ya hada mana kayanmu kamar yadda yai mana a wacan karon da za mu tafi Las Vegas, misalin tara da rabi Nasir ya kawo masa maganin da aka rubutu asibiti, sun dade suna magana waje kamin su yi sallama ya dawo ciki. A gado daya muka kwana kamar yadda muka saba ina cikin kirjinsa har sai da yunwar da dare ta fara damuna na fito kitchen na dora indomie a cikin daren nan domin duk wani abu da ke nan bana sha'awar cinsa ba, ciki kuwa har da kayan marmarin dana ci jiya. Ina cikin zuba magi Aliyu ya shigo kitchen din, hannayensa ya dora a kafata taya ta tayani duba indomie a haka har ta dafu muka ci tare sai ya fini cin ma. “Ashe kai ma kana jin yunwar” “Ba dole na ji yunwa ba” “Ba ka ci abinci ba a gidan Mama Fulani?” “Na ci” Bayan mun gama ya kai plate din a kitchen, ni kuma na nufo dakin domin a falo muka ci abincin indomie. Bathroom na shiga na yi fitsari ko da na fito yana rike da wayarsa da alama kira yake ko kuma karanta sako domin screen din wayar kawai yake kallo na tsawon lokaci sannan ya aje wayar ya zo bayana ya kwanta. Washe gari da wuri na tashi fiye da ko yaushe saboda marmarin tafiyar da za mu yi, Aliyu ne ya hada mana abun karyawa muka karya tare a dinning sannan na shiga bathroom din dakina nai wanka, na saka farin material marar nauyi kamar yadda ya umarce ni, na saka sarka da abun hannu na manta rabon da nai kwallaiya da sarka tun ina karama a lokacin da Mahaifina yake raya ya siya min wata sarka a lokacin karamar sallah, sai kuma lokacin bikina da aka min kwaliya aka saka min sarka, sai kuma yau wani kwarji da kyau sarkar ta kara min kasancewar mai tsada har wani haske ba, kumatuna ya dan kumboro kamar ba nawa ba, mayan idanuwa sun kara fitowa sakamakon cikar da naman idona nai fari na karu sosai har wani shining na ke, ban tana lura da haka ba sai yau da nake kallon kaina a madubi. Murmushi mai wanda ya kara min kyau madaidaicin bakina ya kwanta dan jan bakina da na shafa ya kara fitowa, hannuna na kai na janyo gashina da nai parking a baya zuwa saman wuyana, sannan na dauki wayata ina daukar kaina hoto. Ta cikim madubi na hango Aliyu wanda ya saka wani boyal sky blue kamar na nawa sai dai nawa yadi ne kalar ce kawai daya. Zuwa yai gabana ya tsuna tana ta kallon fuskata ni ko ina aika masa da murmushi mai kyau da saukar da natsuwa. “Kalle ki Babyna kamar ba ke ba” Wannan karon dariya nai ya lumshe idona na bude, ni kaina ina jin cewar kamar ba ni ba ce, ta wani bangaren duk wani abu da ke ta yar min da hankali a yanzu babu shi, na samu rayuwar da ban taba mafarkin samu ba, kuma a cikin sauki ciki kuwa har da saduwar da Mama za tai yau da iyala wanda shi yafi komai faranta min rai a yanzu, da kuma muhunta Asim da za ayi, ga kuma auren Aliyu wanda na san shi ma babban nasara ce a rayuwata domin har ga Allah ina jindadin yadda yake kula da ni yana nuna min kauna, babban abun fargaba ko damuwa a rayuwar aure shi ne samun miji da baya baka kulawa ko kuma baya kaunarka, amman ni ina jin cewar na yi wannan dacen duk kuwa da ban san mi gaba zata haifa ba amman ina jin cewar Aliyu zai iya tsaya min a ko wane hali na samu kaina. Ta dayan bangarem kuma ida na tuna yadda Allah ya daukaka daraja da martabata a take ta ba kuma ta hanyar kowa ba sai ta hanyar mahaifiyata wacce kowa ke gani a wulakance yana raina mu. Lallai bayan tsananni akwai dadi a tafe wani a kusa wani kuma a nesa, a duk inda duhu yake a akwai haske, a tsoro na da rashin gatana na samu kwarin guiwa da gatan da ban yi tsammani ba. Idan na tuna farkon abunda nai ma Aliyu na fasa masa mota da ruwan da ya watsa min a tufafi sai abun ya bani mamaki kuma ya bani dariya, kamar ba mu ba, mutumen da ke kyamar talaka yana ganin kamar ba su da raja yau shi ne a gabana a matsayin mijina har yake yabona ya fada min cewar yana kaunata. Hannuna na ji an kama wanda hakam yasa na dawo daga duniyar tunanin da ke, agogon hannu ya saka min mai kyau sosai sannan ya saka min wata tsarkar hannuna dake tare da agogon, sai yai ma hannun nawa kiss. “I love you both” Ya fada yana min wani lallausan murmushi mai kawata fuskarsa da siffar zatinsa. Goma saura muka fito tare da shi, ina rike da wani jakarta ta rayatawa shi kuma yana rike da karamin akwati kuma ya janyo babban, da kansa ya saka akwati bayan mota sannan ya bude min na shiga kamar yadda na sawa kaina a yanzu ko kuma na ce ya sabar min na bude min mota da kansa. Tun kan yai horn ko yi ma motar key mai gadin ya bude mana gate. “Za mu tafiya zuwa Nijar yau, ban san tsawon yaushe za mu kai a can ba, amman dai ba za mu dade sosai ba, ka kula da gidan da komai, kuma karka bar kowa ya shiga ciki” Ya fadawa mai gadin daidai lokacin daya tsayar da motarsa a gurin da yake. Sannan ya bude wani guri a cikin motar ya dauko kudi masu dan dama ya mika masa. “Ka siya abinci kuma ka yi wata lalurar idan ta taso” Hannu biyu ya saka ya karba yana ta masa godiya sannan ya ja motar kuma nufi gidansu Mama Fulani, kamin mu karasa har Mama Fulani ta kira shi a waya wai ana jiranmu. A harabar gidan ya faka motarsa ta cikin motar ya miko hannu ya bude min kamin ya fita, muma fitowa muka nufi bangaren Mama Fulani tare da shi, a falo muka samu Maryam da Rukaiya da Mama Fulani zaune, Aliyu ya fara sallama sannan ni ma nai, ta amsa mana ita da su Maryam sai dai bata kalli inda ake ba, na gaishe ta ban yi zaton zta amsa min ba na yi zaton yar jiya zata min sai na ji ta amsa min amman salaf da ita gishiri kamar ba ita ba, ta wani sukuku kamar marar lafiya. “Ya jikin naki Mama?” “Al-hamdulillah, Tun dazun ake ta jiranku Ammy ta aiko sau biyu tana cewa na kira na fada maka wanda zai dauke ku ma ya zo” “Okay, Ki yi Mama bankwana” “Mama ina kike karanta bankwana sai mun dawo” “Allah dawo da ku lafiya ya tsare” Shine abunda kawai ta fada bayan an fada mata haka sannan ya mike tsaye ta nufi upstairs, Aliyu kuma ya kalli Maryam da Rukaiya dake zaune a saman kujera suna satar kallon mu. “Allah ya kiyaye ya tsare” Ko wace su ta fada sannan muka fito daga bangarenta muka shiga bangaren Ammy, Mama da Ammy na zaune a falon da kuma Yusuf wato dan'uwana kuma jikan Mai Martaba wanda suka zo tare, Humaira ma na falon ita da Zee da ke ta aikin chatting. Mama na sanye da wata kamfala ja mai kyau sosai kana ganinta kasan mai tsada ce wacce na ke kyautata zaton Ammy ce ta bata domin bata zo da tufafin ba a lokacin da zata baro sokoto ta zo nan. Na gaisa da Ammy kamar yadda na saba Aliyu ma ya gaisa da ita sannan ya gaisa da Mama sai ya fita daga falon yana lasa waya, ni kuma na koma kusa da Mama na zauna. “Ki gaishe shi mana” Ta fada tana nuna min Yusuf da ke murmushi yana kallona, da yaren buzanci muka gaisa da shi yana amsa yana min wasar tabasai kamar daman can ya sani, ni dai ban rama ba domin ban san yadda na ke da shi. Tare da shi muka fito daga bangaren Ammy, hakan kuma be yi ma Aliyu dadi ba, na fahmcin hakan ne ta fuskarsa da na gani a daure yana ta aika min da harara kasa kasa. Kowa ya fito yana mana Allah ya tsare sai mun dawo ciki kuwa har da Maryam da Rukaiya abun babu ko kunya, kuma babu sha'awar gani, ina kyautata zaton sun yi hakam ne saboda kar Aliyu ya ga laifinsu ko kuma Mama Fulani ce ta cilasta su domin ta san Yaran Ammay ma sai sun fito. Aliyu ya zauna gaba ni da Mama muka zauna baya, Yusuf yaja motar muka kama hanya, tsakanin ni da Mama aka rasa wane ya fi wani farinciki da zumudin ganin yan'uwan, ita da ta shekara ashirin rabonta da su ko kuwa ni da zan fara gaduwa da su a yau? Tun da muka shiga motar ni da Mama da Yusuf ne kawai muke magana Mama da Yusuf na yi da yaren buzanci ni kuma sai na maida wata maganar da hausa saboda Aliyu, shi dai be ce uffan ba. Da zahar muka isa lagos, wani kyakkyawan gida aka kai sauke mu, gida ne nadaidaicin mai kyau wanda aka kawata da shuke shuke gwanin sha'awa. A nan muka gaisa da Mai Martaba muka ci abinci muka huta sannan aka zo aka dauki mu aka tafi da mu wani gurin aka dauki hoton mu da tambarin yatsun mu akai wasu abubuwan da ban san ma'anarsu ba sannan aka dawo da mu. Bayan mun dawo Aliyu ya kira Momy ya ba ni muka gaisa har ta ke ce min na kula da kaina kuma na gaishe da kowa da yake can, ya bawa Mama ita ma ta gaisa da ita sannan ya kira Daddynsa shi ma muka gaisa kamar yadda ya fara gaisawa da shi, Abbah ya biyo baya shi da Mama Fulani sai a lokacin ya sanar musu mun iso lagos lafiya kalau. Ba mu bar lagos ba sai da la'asar sannan muka shiga jirgin Mai martaba zuwa nijar, ni da Aliyu muna zaune a kujera daya daga can baya, Mama da Mai Martana kuma suna zaune a wata kujera mai kamar dinning wacce kowa ke iya kallon kowa ga wani dan karamin tebur a tsakani, bayan wadancan jikokin da ya zo da su wato Yusuf da kuma dayan da na ji Nana ta kira sunansa da Abdallah na ga su ma da ban san fuskarsu ba sai yau. Ban san awa nawa ne daga nigeria to Nijar ba, mota balle kuma a jirgin sama, sai dai na yi bachi a cikin jirgin a kafadar Aliyu sau biyu ina farkawa sai kuma nai bachin, abincin da aka ba mu a jirgin kin ci nai duk kuwa da kasancewar na mu ne irin wanda na saba ci yau da kullum amman sai naji bana ma kaunar warin abinci. Aliyu ma Ginger tea kawai ya sha sai wani biscuit na alkama, ni dai ko ruwa da ban sakawa cikina ba har muka sauka. A nan ma akwai banbancin lokaci da can kamar dai yadda mukai wacan tafiyar zuwa Las Vegas sai dai wannan ba tai nisa wacan ba ko kadar nisanta bata kamo ba, wata kila kuma saboda mun sauka da dare ne na ke ganin kamar lokacin da banbanci. Mama da Mai Martaba su suka fara fita daga jirgin tare da masu take masa baya wato fadawansa, sannan ni da Aliyu muka fito sai kuma sauran suka fito. Tun daga yanayin filin jirgin zaka fahimci ba a Nigeria kake ba, domin yawacan mutunen da suk can shigarsu daban ce da wadanda suke airport din Nigeria. Motar biyar aka jera a filin jirgin ban yi zaton na Mai marta ne ba har da na ga ya doshi can wasu fadawan sun fito daga motar da sauri suna tarbarsa, motar da ya shiga dabam da wacce mu muka shiga. Duka motocin bakake ne masu bakim gilashi a hankali suke tuka motar har muka hau babbar hanyar garin. Yawacan mutanen da na ke kallo a titi da inda muke wucewa mafi yawansu suna sanye da rawani da ginuka su sum sha banban da na Nigeria domin su zaka ga wasu ginin na su tun na al'ada ne ba su zamanantar da shi ba, wasu kuma an kawata su kamar garin sokoto. Tun daga unguwar da muka shiga na gane cewar ana yin sarkin a unguwar yadda na ga mutane suna tsayawa kallonsa da daga masa hannu da masa kirari a cikin yaren buzanci. Wata irin katuwar masarauta muka shiga mai haske kamar rana sakamakon kwan lantarki da aka saka ta ko'ina, ga kuma ginin da zanen masarautar irin an al'adar masarautar mai hawa biyu ce, wani bangaren kuma hawa daya ne, ga fadi kamar wata unguwa dukam wadanda suke cikin masarautar daga mai rawani sai mai hula manya da yara, mutane da dama suka fito daga cikon gidan zuwa inda aka faka motarmu suna mana lalle marhabun a cikin kuwa har da manyan mazan da nake saka ran yayun Mama ne, ganinta ya bawa kowa, sai Mai Martaba ya fito sannan ta fito, muma muka fito ni dai sai wara ido na ke abun ka da bakauyen mutum kuma mai son ganin masarauta. Kowa mamakin ganin Mama yake wasu kuma kallonta kawai suke wanda hakan ke nuna cewar ma su kallon nata ba su santa ba ne ko kuma sun manta, domin matasa me ko da yake a akwai manya a ciki, sauran kan mamaki ya hana su magana, ta yadda na ga suna mamakin ne ya fahimtar da ni cewar Mai marta be fada musu cewar ya hadu da Mama ba sai dai zuwan da yai da ita na ba zata. Tare da Aliyu muka karasa gurin da Mama take tsaye shi kan Mai martaba tuni yayi cikin fadarsa tare da manyan amsu take masa baya, Mama kuma ta fashe da kuka har sai da aka rakata a ka shiga da ita ciki. Nima hawayen na ke har muka shiga cikin katuwar fadar wacce akaiwa ado da kwalliya irin ta mutanen da sai dai an zamanantar da adon ta yadda zai burge kowa gwanin sha'awa. Kwatatan fadin fadar da girma ta abu ne mai wahala ga mutum irina ne, domin kallon kwaliyar fadar ya hana ni tsayawa na lura da wadanda suke cikin fadar ma. Ban an kara da hakan ba har sai da masu yi ma Mai martaba kirarin cikin yalshen buzanci suka hankato da ni na dawo daga duniyar kallon fadar. Ashe tuni Mai Martaba yai gaba ni da Aliyu da wasu masu take mana baya tafiya muke zuwa wani bangare na fadar ban sani ba. Duk inda muka bi indai da mutane wasu kallon tausayi suke mana wasu kuma kallo ne akwai ma Mamaki, Mama kan sai aikin kuka take ni kuma ina taya ta da hawaye har muak shiga cikin gidan ni da ita da kuma Aliyu. Shi ka Mai Martana tuni ya kama wata hanyar dabam, Yusuf ne yake mana ja gaba har muka shiga inda Mata da yaya da yawa suke. A tsakar gidan Mama ta gurfana ta fashe da wani sabon kuka mai taba zuciya, matan gaba daya suka zagaye ta suna kallonta kamin wasu su kama ta su shiga da ita ciki ciki. A bangaren da ke farko aka shiga da ita wanda na ke kyautata zaton na mahaifiyarta ne ganin hoton Mai Martaba da wasu da ga kuma wati dattijiwa wacce tuni ta kawo bakin kofar falon tana kuka sosai har da saka hannunta ta dafe zuciyarta, Mama ta fadi a bakin kofar tana rike da hannun matar matar ma ta rike hannun Mama gam tana kuka sosai, ba ni kadai ba kowa da ke gurin sai da ya tausawa Mama da matar saboda kukan da suke da kuma wasu ma har da kukan sai da sukai. “Nana ce ta dawo, Nana ce, Nana, Nana” Shine abunda yawancin matan da ke gurin suke fadi tare da wasu dattijan mazan, wadanda suka tsaya rumgume da hannunsu suna kallon Mama. Sai da akai ta ba su hakuri sannan Mama ta tsagaita kukan da take ta shiga cikin katon falon wanda sanyin ac da kamshin turare ke maka lale marhabun. Muma shiga cikin falon ni da Aliyu sai aka dawo kan mu ana ta kallon mu wasu har da bude baki, ina jin lokacin da wasu ke fadar ni da Aliyu duka yayanta ne wai Aliyu ne yaya ni kanwa, wasu kuma su ce rakota mu kai. A lokacin da Dattijiwar ta zauna a falon sai ta daga kanta sama hawaye nata mata zuba sai girgiza kai take. “Mama ki yafe min, Mama ban kyauta miki ba aikata daidai ba, kuma ban kyautawa kaina ba na sani, kuma na cancanci ko wane irin hukunci ko fushi daga gareki” Mama ce take fadin haka tana daga kasa zaune rike da hannun matar tana kuka, matar ma kukan take irin na tsofi gwanin ban tausayi da taba zuciya, ta hanyar kalaman da Mama take na fahimci cewar dattijiwar Mahaifiyarta ce duk kuwa da kasancewar ba a su yi kama sosai ba domin Mama ta fi kama da Mai Martaba. RAHMA POV. daga idonta har makoshinta da fatar jikinta abushe suke kamar wacce. Ta shekara ashirin a gadon asibiti, kallo daya zaka mata ka fahimce akwai damuwa sosai a cikin zuciyarta, tun daga lokacin da aka kawo ta asibiti ta farka bata ce da kowa komai ba, ciki kuwa har da mahaifiyarta da ke kai da kawo tana yawan tambayarta idan tana bukatar wani abun, sai dai ta gyada kai ko ta girgiza, likitan da ya zo dubata ma sai dai ta girgiza masa kai ko ta gyada kai, rashin maganar ya damu kowa domin an kasa gano matsalar rashin maganar tunda tana ji maganar ce kawai bata furtawa, wata kila damuwarta da ke ranta ce ta hana ta magana da kowa ko kuma wani ciwon ne, na daban ya same ra a yanzu. “Ya kamata a sanar da mijinta Mommyn wannan abun, tun da ta tashi ba tai magana ba, idan kuma aka takura da magana ta fara hawaye wannan abun yayi yawa” “Ya san da ita ai, tun da yai aure be waiwaye ba, idan ma ya zo ba wani maganin zai mata ba, koda ce take bukata kuma ta mu In-Sha-Allah” Mahaifiyarta ta mayarwa da Ikram amsa cikin hawaye, kallonsu kawai Rahma ke yi ba tare da tace komai ba. “Ko jiya ya kirata amman ban daga ba saboda ban san mi zan fada masa ba, amman kyaleta a haka ba shine mafita ba, ya kamata ace ya san matarsa tana asibiti ko da ba zai mata komai ba” “Idan ya kira ki daga ki fada masa cewar matarsa bata da lafiya tana asibiti” “To Mommy” Mommyn ta fice daga dakin cikin damuwa tana share hawayenta. Rahma ta bita da kallo, irin kallon na tausayin mai jinya idan yana jinyar kansa, tana son mahaifiyarta kamar yadda mahaifiyarta take sonta, zata mata sadaukardar da take jin ba lalle ne ta rayu bayan an dasa mata kodar ba, zata iya mutuwa bayan cirewa mahafiyarta kodar an sada mata ya zama an yi ba ayi ba kenan! Abu daya take da bukata a yanzu mutuwarta kamin a cire kodar mahaifiyarta a dasa mata, domin ta san zata bar duniyar komai daren dadewa, and mutuwarta zata fi mata rayuwarta a yanzu, domin bata da tabbacin idan an dasa mata wata kodar za ta rayu. Abu daya take fata kuma take ta jira a yanzu zuwan mutuwarta kamin jibi da mahaifinta ya fada mata za a fita da ita waje ayi mata aikin kodar a can. “Rahma?” Ta juyo ta kalli Ikram tana hawaye kamar yadda yar'uwata take yi. “Dan Allah ki cire damuwa a ranki ki yarda da duk abunda ya same ni daga Allah ne kuma babu mai iya miki maganinsa sai shi” Kai kawai ta gyada mata ta hade yawun bakinta. Alama tai maga da ta bata wayarta sai ta ciro wayar daga jakarta ta mika mata. Kamar hadin baki tana karbar wayar kiran Aliyu na shigowa wayarta da layinsa na Airtel. Kara wayar kawai tai a kirjinta ta lumshe ido tana hawaye. “Ki dauka mana idan ba za ki iya ba ki ba ni” Mika mata wayar tai ita kuma ta koma ta kwanta saboda numfashin da taji yana yin sama sama kamar zai fita daga jikinta. Ikram ya dauki kiran ta saka wayar a hands-free tana kokarin danne kukanta. “Hello Dear” “Ba ita ba ce, Ikram ce” “Ina Rahma?” “Tana asibiti tun shekaranjiya” Ikram ta fada cikin kuka. “Mi ya same ta?” “Ciwonta ne ya taso har bata iya magana” Sai kawai ya kashe wayar, Rahma har lokacin kuka take marar sauti tana dafe da zuciyarta gwanin ban tausayi, ga jikinta babu sauran karfi. *Ayi hakuri a gafarce ni, dukan wani tsaikon da ke sakani typing da dare na gama shi yau, Al-hamdulillah. In-Sha-Allah posting din dare ya kare da yarda Allah.* *Ina mata son rage kiba? Ina mazan da kiba ta hana su sukuni? Ina masu jikin yai kyau kamar na yarinya? Ina masu fama da kujera ko wani ta bo a fuska? Ina masu fama da hawan jini? Masu diabetic? Ag cera an gwada yayi an tantance ingancin babu shakku ko kadan. AG cera ya zo domin ya temaki garkuwan jiki da kuma lafiyar jiki. Sinadari ne wanda ze magance matsaloli da dama wadanda suke hana garkuwan jiki aiki yadda ya kamata ko kuma yake rusa garkuwan jikin ita kanta.* *Cututtukan zamani daban daban sun sa mutane gaba kuma magance su yana da wahala; irin ciwon Sugar, hawan jini, ciwon sanyin kashi, ciwon gabobi da sauran su. Haka ma cutukka irin wadanda suka shafi fatar jikin wadanda sun hada da kyasfi, pimples, takurewar fata, rakainuwar fata da kuma haske da kyallin fata duka ana shan AG cera kuma yana temakawa wajen magance illolin nan. Mutane masu fama da rashin karfin jiki wajen kwanciya da iyali da kuma mata masu fama da yawan ciwon mara lokacin al'ada ta karshen wata suma baa bar su a baya ba. A takaice dai AG Cera yana temakawa wajen magance cuttukka daban daban wadan ke damun mutum. Domin karin bayani ku tuntuni mu a wannan number +60167474649 ko kuma ku ziyarci shafin mu http://agnutritioninternational.com.* Daker Mama ta tsagaita kukan da take, har suka samu damar magana da juna. “Babu wanda ya fada min za ki dawo, na yanke kauna daga ganinki na dauka kin mutuwa gaba daya, ko kuma kin tafi kin tafi kenan ba zan sake saka ki a idona ba” Mahaifiyarta ta fada tana hawaye, Mama kan kasa magana tai sai hawaye take, wani da na ke kyautata zaton Yayan Mama ne ya ce. “Dukan mu mun san da maganar kawai dai mun boye miki ne saboda Mai Martaba ya bukaci haka, mun san idan har kika sani za ki damu kanki sai kin ganta kuma ki katsa natsuwa” Hannun Mama kawai take murjawa tana hawaye da motsa baki irin wadanda kuka yake cinsu. “Nana Asma'u tana can ta kafa wata sabuwar rayuwar har ta yi ya ta aurar da yarta ba tare da sanin kowa ba, wata kila da Mai Martaba be ganta ba, da ba zata dawo garemu ba” “Ina jin kunyar abunda na aikata, ina jin cewar ban yi daidai ba, shiyasa ba zan iya dawowa ko tunkarar kowa ba” Mama ta fada sai Mahaifiyarta wacce zan iya kira da kakata ta daga kanta tana kallon inda na ke har tana girgiza kai alamar mamaki da takaici abunda aka fada mata a yanzu. Ba mutanen gidan kadai ba, har da wadanda na ke ganin kamar daga wata unguwar suke shigo duk wanda ya shigo ya ga Mama sai ya fashe da kuka kuma yai mamaki, hakan na nuna cewar an dade da shafe tahirinta a cikin gidan ne, wanda ya santa ya san wanda kuma be santa ba sai dai a bashi labari wata kila ma wanim ba za a fada masa cewar masatautar na da wata Gimbiya mace daya ba, sai abun bakinciki a alakanta Gimbiyar da guduwa saboda soyayyah. Mun yi awa biyu a gurin sannan aka kai mu masauki, na yi zaton dabam za bara mu sai gashi an sauke mu daya daya  a wani bangare na gidan ni da Aliyu.   Sallah ce ta zame nana wajibi sai da muka sauke nauyinta sannan na fara shiga a bandakin da aka tanadar masa komai kamar an san da zuwanmu. “Babyna” “Na'am” Na amsa daga can cikin bandaki sai kuma na leko domin na riga da na cire tufafin jikina, tawul ya miko min ban san da yayi gurinsa ba sai yanzu, karba nai ya turo kofar sannan na fara kunna ruwan, ban wani dade ina wa kam ba na fito, ko da na fito Aliyu ya hada min tea a cikin kayan tea da aka kawo mana da kuma abinci. “Ki fara shan wannan kamin ki ci komai kar cikinki ya kumbure” Sai da na zauna a bakin gadon da yake zaune sannan na mika hannu biyu zan karba, sai da ya shafi hannayen nawa kamin ya sakar min cup din ya nufi bathroom. Sai da na saka doguwar riga na gama shirya kaina sannan ha fito daga wankan. “I can't wait na ganki da cinin cikin nan, abun yana burgeni fa” Ya fada yana gyara daurin tawul din dake kogunsa, ni dai ban ce komai ba domin tuni kunya ya sauko min, ni wani lokacin har mamakin yadda Aliyu yake fadin wadansu maganganu nake ko aikata wani abun ba tareda kunya ba. “Sauka kasa ki ci abinci” “Kai ba zaka ci ba?” “Zan ci mana, kin san dai ke a jirgi ba ki ci komai ba yunwa tana tare da ke, idan kuma ba kya bukatar wannan kalar abincin sai a siyo miki wani” Na saka masa dariya jin irin karfin halin da yake da shi. “Ka san garin ne da za ka siyo min wani?” “Dole sai an san gari ake yawo? Ga waya kuma zan iya bin hanya ina kallon abubuwa ina karantawa har na isa, ko kuma nai ta tambaya har na dace” “Idan kuma ka bace fa?” “Sai Mai Martaba ya saka cigiyata, surikin masarauta ya bata kuma ga jikarsu da ciki” Ya fada kamar ba shi yai maganar ba. Nikan dariya ce aikina har ya saka tufafinsa ya zauna kusa da ni, a tare muka ci abincin ba laifi ina sha'awar abunda aka kawo mana kuma na ci sosai, kamin a bugo kofar dakin wai na fito ana son ganina. A yadda yanayin Aliyu da fuskarsa suka nuna kamar be jidadin kiran nawa ba, domin a ganinsa mun yi tafiya mai nisa haka kamata yai ace mun huta musamman ni da yasan ina da cikin na san wannan baya rasa nasaba da abunda ya saka yake kin bari na nai wata tafiyar ni kadai. Ni na fara fita na gaisa da wasu da aka fada min cewar iyayena da kuma kawunnai na sannan aka saka na dawo na kira Aliyu shi ma suka gaisa da shi. Bayan sun wuce shi ya koma dakin da aka sauke mu ni kuma na bi wata buduwar gidan na ce ta kaini dakin da Mama take. Ban same ta a falon ba sai wasu yan mata da suka fara bachi akan kujerar, har cikin dakin Hajiyar aka kai ni a nan na samu Mama zaune mahaifiyarta kuma a tsaye tana rike da wata sandar karfe wacce na ke kyautata zaton tana taimaka mata ne a tsayin ko tafiya. Ina shigowa sai suka maida kallonsu gurina dukansu kana ganin su ka san suna cikin damuwa ba kuma damuwa ta bakinciki ko zullumi ba ta nadamar abunda ya faru da kuma ganin junansu ta inda ba su yi tsammani ba. “Ace wai ki gina wata rayuwar a can har ko aurar da ya ba ki nemi familynki ba” Mahaifiyarta ta fada tana kallona har na zauna kusa da Mama. “Auren ya do mana ta inda ni da ita ba mu yi tsammani ba, kuma ko da ace an dauki lokaci kamin auren bana jin cewar zan ka kawo mijinta ko ita ta ganmu saboda na san abunda na aikata” “Wa ake aikatawa laifi be yafe ba? Allah ma muka masaba daidai ba yafe mana balle mu? Na san kin aikata kuskure amman Mai Martaba ma bayan tafiyarki ya ji cewar be aikata daidai ba ta hanyar nuna cewar zai aura miki wanda ba ki so, shi kan shi abun ya dame shi domin da be yi hakan ba da duka komai be faru ba, da yanzu wannan ciwon zuciya da na ke fama da shi na ki be same ni ba, da yanzu kina nan cikin yan'uwanki ana yin komai da ke, a duk lokacin da kowa ya taru sai na ji kamar ace kema kina nan, idan jikoki suka taru sai na tambayi kaina ko ina nake suke wane hali kike a yanzu, a mace ko raye ko kuma a cikin wata mummunar rayuwa” “Ba laifi ba ne dan uba ya zabawa yarsa ko dansa abokin rayuwa na gari, Mai Martaba ba aikata laifi ba, kuma be yi hakan dan ya jefa rayuwata a matsala ko damuwa ba, yayi hakan ne saboda al'adar gidan nan ce, ni kuma sai na bijire na gudu na bar muku abun kunya da magana a gari, soyayya da kurciya a wacan lokaci ta debi da yawa har na kasa gane cewar abunda na ke kokarin aikatawa babban abu ne kuma be dace na aikata hakan ba, a lokacin dana farga daga abunda na aikata kuma sai na ga lokaci ya kure min ba zan iya gyara komai ba, amman na gode Allah daya ba ni ikon neman yafiyarku a lokacin da na ke da rai kuma kuke raye, Wallahi ba zan iya kwatanta irin farincikin da jindadin da na ke ciki ba a tsakanin lokacin da nai arba da mai martaba da kuma ganin ki a yau” Mama ta fada tana hawaye. Sun dade suna tataunar magana tun tana a tsaye har ta kai g zaunawa, tana sako labarin Babana wai ai ga fuskarsa nan a fuskata, a lokacin da Mama ta bata labarin cewar tana da wani dan bayan ni wanda ya rasu sai da Kakar tawa tai kuka, sai dai Mama bata sako mata labarin ciwon kodarta ba a cikin labarin da ta bata. Ban bar dakin sai da na fara jin bachi kusan ma a cinyar Mama na fara shi sai da ta tashi ta ce na koma wai na baro mijina can shi kadai. Sannan na tashi idona da kufan bachi na dawo inda aka sauke mu kamin na iso har na gaji domin akwai tazara sosai a tsakanin bangaren matan sarki da kuma inda aka sauke mu. Ban yi mamakin samun Aliyu a farke ba, daman ban kawowa raina cewar zai iya kwantawa ba tare da ya gan ni na dawo ya tabbatar ni na fara yin bachin ba, hakan kuma ba karamin dadi yake min ba. Na yi zaton ko zai yi magana ya ce yaje na zauna na barshi a gurin, sai na ji shiru be ce komai ba kamar ma hankalinsa yana wani gurin. Bandakin na shiga nai fitsari na fito ina hamma har da hawayen bachi na cika min ido na ce. “Baka kwanta ba?” “Ba zan iya bachi ba sai na tabbatar ke kika fara yi” Hawa saman gadon nai ba tare da na ce da shi komai ba. “Ba za ki canja tufafin jikinki ba?” “Bachi na ke ji sosai” “Na canja miki?” “A a ka bar su hakan nan” Tashi yai yaje ya rufe kofar falon sanna ya dawo ya tura ta dakin sai kuma ya kashe wutar ya bata bayana ya rumgume hannunsa a kan ruwan cikina. “Babyna gobe zan koma” Ya fada min kamar mai rada bakinsa daidai kunne na. “Miyasa baka son zaman nan ne?” “Ina son na ga yan'uwanki su san ni na sansu, amman tafiyar ta dole ce” “Miya faru?” “Rahma bata da lafiya, ina bukatar na je na dubata” A take bachin da nake ji ya wartsake wani abun na ji ya soke ni a cikin zuciyata wanda ban taba jin irinsa ba. “Ko kadai kana neman wani uzurin ne daman?” “Ko kusa, tafiyar ta zame min dole ne tun da ciwo ne ke damunta, ya kamata na je na dubata” Shiru nai ban ce masa komai ba, sai dai ban jidadin ko sunanta daya ambata ba balle kuma zancen dubata, wata kila shi ya kitsa haka saboda na bishi mu koma ni kuma bana jin zan yi haka, ko kuma yayi hakan ne domin ya koma wata kila kuma ita ce ta tsara hakan saboda ta samu damar da zai dawo ya baro nan ko kuma ta hargitsa mana tafiya ko wani abun da dabam da ban san ma'anarsa ba. Ni kan har na manta da yana wata mata wai Rahma ashe fa Aliyun ta ne nake aure, ko tana ina ma iho ban sani ba, kuma ban ji zan iya tambayarsa ba domin bana son ji wani abun daya shafi sunanta ma balle kuma ita din da kanta. “Ki min alkawarin kula da kan ki pls” Ya fada yana sumbatar saman kaina, sannan ya juyo da ni ya shiga aikawa ko wane bangare na jikina da sako. Mun farka da wuri sakamakon kiran sallah asuba da ya tashe mu wanda ake yi aciki masarautar, sai da ko wannen mu yai wanka sannan mukai alwala shi ya fita zuwa inda yake jin karar loudspeaker masallacin na fito ni kuma nai tawa sallah a cikin dakin, ina ta tunani ta inda ya ji cewar Rahama bata da lafiya bayan ma layin Nigeria ba yayi a wata kasar kamar yadda ya fada min, kwata kwata zancen tafiyar nan be min dadi ba, wata kila saboda na saba da shi ne ko kuma saboda Rahma zai je gani yasa na ke jin ba dadi oho ba dai zan iya fadar dalili ba.   Bayan an gama sallah da kamar minti talatin sannan ya shigo inda na ke. “Good Morning” Ya gaishe ni tun kamin na mika masa tawa gaisuwar, nikan kasa amsawa nai sai kawai na gaishe shi da halshen hausa sai ya amsa min yana kissing goshina. “Lafiya kalau, kin tashi lafiya?” “Lafiya kalau” Hannunsa ya miko ya kama nawa. “Ta so mu kwanta ina son kiji dumi jikina kamin anjima” “Da rana zaka tafi?” “Ban sani sai an bincika min idan akwai jirgi” “Wa zai bincika maka? Taya ina ma ka ji bata da lafiya?” “Na kira wayarta ne, sai Yayarta ta dauka ta fada min” “Amman ka ce layin Nigeria ba yayi a wata kasar” “Yeah ban da Airtel na can yana yi a nan, har daga saudiya ma ina kira da Airtel, na saka Nasir ya bincika min, ke kuma yanzu ina son ki fada musu zancen tafiyar idan mun shiga gaishe su” Na gyada masa kai kawai ba tare da na ce komai ba. Kamar yadda ya fada na ji dumi jikinsa sosai ta a kuma wanin abun mukai ba bayan dogon bachin safe normal sleep, sai dai yadda ya shigar da ni jikinsa ya rumgume ya saka na jidadi kuma na ji dumi da yake fada. Misalin tara aka kawo mana abincin karyawa tun daga kan shigar masu kawo abinci za ka tabbatar da cewar bayin gidan ne, domin sukansu suna sanye ne da tufafi kala daya sun jero kamar tururuwa. Duk yadda ya so na ci abinci sosai sai na kasa, sakamakon dadin da raina baya min kan tafiyar da zai yi. Sai dai na yi kokarin boyewa domin ni ma ban ga abun damuwar akan zai tafi gurin matarsa ba. Daya daga cikin yan matan gidan aka aiko wai na shirya na fito ni da mijina za mu je mu gaishe da Mai martaba da matan gida. Ni ce kawai nai wanka na shirya shi Kan Aliyu tun kamin mu fara karyawar yai wanka ya shirya.   Rana ta fito sosai ko da muka shiga bangaren Mai Martaba tare da mai mana iso, na yi zaton wani gurin dabam za a kai mu inda Mai Martabar yake kebe sai ga mu a fadarsa ta jiya duka iyalansa da hakimansa suna ciki ban da shi. Muna shiga sai idon kowa ya dawo kan mu “Zo nan ki zauna” Wani Dattijo ya fada yana nuna min inda zan zauna din a kusa da shi. Ni da Aliyu muka zauna a kasa sai ya fara nuna waenda zan gaida sune iyayena da kuma abokiyar zaman kakata, da kuma sauran da suke yan'uwana  wasu dai ban ga fuskokinsu a jiya ba, sai yau ina kyautata zaton zuwa su kai a yau, sai haba haba suke da ni da kuma Mama. Duka zuri'ar Sarkin farare tas wasu ma har sun fini fari da jar fata, ga kyau kamar larabawa daga mayan har yara da matashi farare ne, sai dai wani ya fi wani farin, a cikin hakimansa kuma akwai fafaren da bakeke, matanyen na sanye da shadda ga wani uban ginari a hannu da wuya ko wacce ta saka gwanin sha'awa. A lokacin da sarkin ya shigo sai da kowa ya mike tsaye masu kirari ta bude rigunansu suna tare masa gaba da baya suka fara wasu kuma na fita da katon mafecinsu. Yadda ake ma sarkin sai da abun ya burgeni kuma ya kara min jindadi. Sai daya zauna sannan kowa ya zauna, da dai daya masu rawanin suka fara zuwa suna mika masa gaisuwa baya amsawa sai dai badawansa su amsa a madadinsa har suka gama gaisuwar.   Sai da yao gyaran murya sannan yai dan jawabi akan dawowa Mama da kuma zancen yafiyar da yai mata, sannan ya sallami wadanda ba familynsa ba ya bar iyalan gidansa kawai ya sake gabatar musu da jawabi tare da nasiha da kuma jan kunne akan al'amurran rayuwa, fada musu abubuwan da ya samu Mama na bijire musu da tai a ciki har da zancen cire mata koda wanda kowa be san da maganar sai a yau. Babu wanda be girgiza ba da jin lamarin kuma aka tausayawa Mama, duk na san ba za a rasa wadanda a zuciyarsu za su ce Allah ya kara ba domin ita ta jawa kanta. Hankalin kakarmu ya tashi sosai jin cewar an cirewa Mama koda sai dai Mai Martaba ya shaida mata ya jaddada mata kuma ya tabbatar mata da cewar za a kwato mata hakkinta domin tuni elya mika abun ga kungiyar likitocin kasar, ko zuwan nan da zai yi sai da ya roke su akan su daga mana kafa ta samu zuwa ganin danginta kamin su gama tattara bayanai.    Yayi takaici kuma ya nuna bakincikin akan abunda ya faru da kuma gina mana rayuwa da tai ba tare da yan'uwanta ba. Sai dai abun jindadi kuma mai muhimmanci dawowarta a yanzu wanda hakan zai ba ni damar sanin yan'uwanta da kuma yan'uwan mahaifina kamar yadda sarkin ya fada.   Bayan ya gama jawabinsa ne aka sallami kowa, ni kuma sai na raba kusa da Mama na fada mata cewar Aliyu yana son na koma yau saboda Rahma bata da lafiya, ita kuma ta fadawa yayanta yayanta kuma ya samu Mai Martaba ya fada masa a take, Mai Martaba ya sa a bincika masa idan za'a samu jirgi da a yau, aka tabbatar masa da babu sai dai gobe, saboda haka dole Aliyu ya aje tafiyar har gobe.   A ranar aka kai ni gurin kakannina na bangaren uba, ganin cewar Aliyu zai tafi ba masanar ko ya dawo yanzu ko kuma sai nan da kwana biyu ko wani lokacin, su kansu ba za su jidadi ace ya tafi ba tare da sun ganshi ba, kuma za su iya daukar cewar saboda su suna takalawa ne, tare da Mama muka tafi da kuma wasu daga cikin yan gida, akwai tafiya mai nisa sosai tsakanin unguwar da Sarkin yake da kuma inda su suke. Ko da muka isa rana ta bude sosai a unguwar su har sun sauke sallah azahar. A hanyar mu ta zuwa ne na ke labartawa Aliyu jawabin da sarkin yai abubuwan daya fada, domin duka maganganun da yai da yaren buzanci yai shi wanda kuma Aliyu ba ji yake ba. Sai da aka fadawan ta Mai Martaba ya hado mu da su suka shiga aka sanar sannan mu ka bi baya. Gidan kasa ne gaba daya gidan, sai dai irin ginin nan ne na mutanen da wanda ake na iyali da yawa, wanda zaka samu wani lokacin har da jikoki ma a gidan. A gidan muka wuni ni da Aliyu suna ta kiran mutane a zo a ganmu wai yar Ummaruje ce kamar yadda take fada, tsohuwar ko gani bata yi sosai Nene na ke jin suna kiranta, ta yi farinciki sosai da ganin mu kuma ta yi kuka ita da duka yan gidan jin cewar Baba ya rasu, ba su kadai ba ni kaina sai da nai kukan tunawa mutuwar tasa, yau ga ji a gaban iyayensa amman babu shi. Sai da dare muka baro gidan a can muka ci abincin rana da dare da za mu dawo aka tasa min nonon rakuma saboda an bani na sha na jidadi har na roka. Kallo daya za ka ma fuskokinsu ka fahimcin cewar suna cikin farinciki da jindadi ganinmu, ban yi zaton Aliyu zai sake jiki kamar yadda yai a yau ba, fuskarsa na nan a yadda take babu wani walwala sosai Murmushin ma ba komai yake ba, amman ya sake jiki ta hanyar cin abincin da aka kawo mana da har ma da Nonon ragumin wanda ya fada ai yana shansa a gidan Mama Fulani wani lokacin tana siye ta aje. Duk kuwa da kasancewar an aiko mana abincin daga masarautar suna ganin kamar ba za mu iya cin wannan ba, wani abincin ma na san saboda Aliyu aka girka shi irin tuwon shimkafa miyar Allayahu da akai da man shanu ga naman kaji da garo a ciki. Ba tare muka dawo da Mama ba domin ita tana gama gaisawa da su ta dawo gida, wai bata son kowa da kowa ya zo ganta ta san ba zasu taba cire tabon abunda ta jawa musu na ja  dansu su gudu ba, ballantana yanzu da ta kawo musu labarin mutuwarsa har a bada ba za su manta da ita ba, ba kuma za su yafe mata ba, duk wani so ko nuna mata kauna da za su yi ta ciki na ciki tana ganin kamar komai lafinta, saboda ita taje ta same shi da zancen guduwar kuma ya amince.   Na dawo ima jin kamar kar na baro na dawo nan ba, ba dan komai ba sai dan yadda tsarin gidan da kuma yadda suke haba haba da ni ya burgeni, har ta ginar gidan ana ta lekowa ana kallona, ba ma kamar lokacin da za mu tafi har da masu fitowa suna kallon motocin Mai Martaba.   A cikin unguwar na yi ta ganin zangon maza masu shan shayi da yar butarsu wasu sun yi gugun guri daya sun kuna kidan buzaye wasu kuma suna ta fira abunsu. A lokacin da muka dawo gidan ma sai aka sake kawo mana wani abincin aka ni dai sai da na ci Aliyu ne kawai be ci ba saboda ya koshi, muna shirin kwanciya aka aiko kirana, har zan fita haka sai ya rike ni ya dauko min Hijab. “Gidan nan har ya fi gidan mu yawan maza, bana son fitar ki haka Baby, kuma ya zama dole ki min alkawarin kula da kanki da jikinki da kuma babyna da yake cikin ki kamin na tafi pls” “Taya mutum zai kula da kan shi? Da ma dai kula da wani ne ai zan iya” Ya kama kunkuruna ya rike. “Karki bar kanki da yunwa, ko kuma wani abun ya same ki, idan kin ji ciwo ko rashin lafiya ki yi saurin fada, kar ki bar jikinki haka nan sake har wani ya ga kyauki ko ya yaba, ki rika rufe jikinki kina tunawa cewar ke ajiyar wani ce” Na gyada masa, sai ya sumbance ni sannan ya sake ni na fita. Bangaren da Mama take na nufo sai dai ban same ta a dakin dana same ta jiya ba sai wani dakin dabam,tana tare da mahaifiyarta da kuma wata mai kula da gidan da kuma wasu matan da aka nuna min dazun da safe aka ce matan yayyen mahaifiyata ne. “Saboda tafiyar safe zai yi ya kamata ki fada mana abunda yake bukata sai saffara masa da wuri kamin ya tashi” “Wa? Wai Aliyu? Okay bari na tambaye shi” Duk kallona sukai har Mama dakanta kamar na yi wani sabo ko fadin maganar da ba daidai ba. Sai Mama da sauran matan sukai murmushi. “Ina ruwan Ataa” Mama ta fada. “Mu a nan ai ba a fadar sunan miji, miji yana da girma sosai, kuma akwai kunya ka fadi sunan miji kai tsaye, ina ma laifin ki ce masa Hamma” Cewar Mama Hajjo. Sai a lokacin na gane dalilin kallon nawa da suke, ashe dan na fadi sunan Aliyu ne kai tsaye. “Ga ki da sunan Maman su Mai Martaba amman ba ki iya girmama manya ba?” Na yi kasa da kaina alamar kunya sannan na fice. Lokacin da na dawo dakin ya same shi rike da waya a hannu, ina shigowa ya dago kai yana kallona. “Hamma wai ance mi kake so a maka da safe kamin ka tafi?” Na yi maganar da sigar zolaya ina dariya tare da lake kafada kamar karamar yarinya. Murmushi yai ya miko min hannunsa. “Zo nan matar Hamma” Sai na saka dariya na zo gunsa kamar yadda ya bukata. Sai ya dora ni kafafuwansa. “Wace ki ce min Hamma” “Cewa akai wai ba a fadar sunan miji, shine aka ce ina laifin na kiraka Hamma” Na fada ina dariya, sai shi ma yai dariya. “Ke kuma na rika ce miki indo” “Eh na yarda, fada min abunda kake so aka dafa maka da safe” “No bana bukatar komai zan karya idan ya sauka can, akwai kayan tea a nan zan iya hadawa na sha ai” Haka na koma na fada musu baya bukatar komai, sannan na dawo bangaren mu muka kwanta. Washe gari..... Ina gama sallah asuba na kunna butar ruwan zafi na hada masa tea, ko da ya shigo ina saka masa sugar. Be sha ba sai da ya bani na fara sha sannan ya sha, sai ya tashi ya shiga wanka ya fito ya shirya nima na shiga nai wanka na shirya. Har airport na raka shi ina jin kamar kar ya tafi saboda na saba al'amurarransa kuma ina ganin kamar tafiyar tasa bata zame masa dole ba, wata kila saboda ya baro ni ya dawo ne tace wani bata da lafiya. A lokacin da zai fita motar sai da nai masa kuka domin har ga Allah ban jindadin tafiyar da zai yi ina jin kamar na bishi amman ba hali. “Ki samu layin kasar nan ki saka a wayarki ki kirani kinji? Ba zan dade ba zan dawo matukar jikin nata da sauki zan dawo na ga sauran yan'uwanki” Ya fada min murya kasa kasa, ni kuwa ina lafe a kirjinsa ina hawaye. “I love u ki kula min da kanki pls” Ya fada bayan ya bude motar ya fita sai na gyada masa kai ina hawaye. “I love you” Na fada masa kamar ba ni ba, dawowa yai cikin motar ya saka bakinsa cikin nawa na tsotse yawuna sannan ya cire ya sunbanci goshi sai kuma yai kasa ta hannunsa ya shafa cikina. “I Love you More” Haka muka rabu ina jin kamar idan ya tafi ba dawowa zai yi ba. ALIYU POV. Da zahar jirginsu ya sauka Lagos, hutun awa daya yai wanda hakan ya ba shi damat kiran Momy da Mama Fulani ya fada musu cewar ya dawo yana Lagos kuma zai kama hanyar sokoto saboda Rahma bata da lafiya, Momy ba tai mamakin jin cewar bata da lafiya ba daman ta san za a rina wai an sace zanen mahaukaciya, ta san inda ta ji Ataa na ta ciki kuma ga rufin asirin da suke takama da shi na kakanta ne dole ta kwanta ciwo. Daga Lagos ya hau jirgi zuwa sokoto, daman tun yana nijar yayi waya da Nasir ya sanar masa a samar masa ticket a cikin jirgin da zai je sokoto yau, ta online Nasir ya masa komai. Da magariba ya sauka sokoto, sai da ya kira Husna ta kawo masa mota sannan ya nufi masallacin gurin yai sallah, after ya gama sallama ya sai da ya dan jira sannan Husna ta iso, daga airport din ya wuce asibitin Uduth, kamin ya isa ya kira wayar Rahma wata daga cikin yan'uwanta suka dauka suka fada masa dakin da take.   Ya shiga asibitin a lokacin da ba a shiga sai dai sanayyarsa da wasu likitocin ciki har da Doc Bukar ya saka an barshi ya wuce tare da Husna. Daga Rahma sai kanwarta Zulfa da mahaifiyarta ne a dakin. Hankali a tashe Aliyu ya shigo domin tun jiya jikinsa na bashi ba lafiya ba. Idonta a rufe suke amman tana jin muryar mijinta ta bude ido tana kallonsa, Mahaifiyarta na amsa gaisuwar Aliyu ta fice daga dakin. Sai ya rage daga kanwarta Zulfa sai Aliyu sai Husna. Cikin sanyin jiki Aliyu ya karasa inda take ya zauna a saman kujerar yana kallonta, gaba daya bakin idonta ya bace bat, sai farin kawai shi ma kuma kamar ba daidai take kallo da shi ba, fuskarka da fatar jikinta sun bushe sosai kamar wacce ta dade bata da lafiya. “Mi ke damunta?” “Ciwon kodar ne, sun ce idan ba a canja mata ba a yan kwanakin aka mata dashen wata zata iya mutuwa, amman Mommy tace zata bada tata daya, gobe da maraice ma za a fita da ita zuwa inda za ayi aikin a London” Juyowa yai ya kalli Zulfa cikin bacin rai. “Akan me ba za a kirani a fada min bata da lafiya tun a aka kawo ta asibitin? Da ban kira ba da ba za a kirani a fada min ba kenan? Ni fa mijinta ne ina da hakki da yawa akan ta, kuma hakkina nema mata lafiya ba na iyayenta ba” Zulfa ta yi shiri bata ce komai ba, sai ma saurin ficewa da tai daga dakin ganin yadda ran Aliyu ya bace sosai. Husna ma ficewa tai gudun kar ita ya shafe ta dan tasan halin yayanta be iya bacin rai ba. Hannunsa ya kai ya kama hannunta, kamar jira take sai ta jimke hannunsa da karfi tana ta kallonta hawaye na sauko mata. So take ta masa magana so take ta nemi yafiyarsa kuma ta fada masa wasu abubuwan amman bata da wannan damar domin an iyakance mata maganar tun daga lokacin da tai wacan faduwar, ashe furta magana ma ba yin bawa ba ne na mahallincinsa ne sarrafa halshe ka iya fadar abunda kake so ma ba ikon mai shi ba ne iko ne mahallincin halshen da mallakin jiki gaba daya. Hannunsa ta ja ta rumgume a kirjinta Aliyu yai saurin ciro wayarsa ya kira Muhseen. “Muhseen dan Allah ka taimaka min ka zo yau if possible ka duba Rahma kamin a wuce da ita tana jin jiki sosai” Shiru Muhseen yai na wani lokaci kamin ya ce. “Gaskiya ba yau ba, sai dai gobe idan an samu jirgi” “Da safen pls” Aliyu ya fada idonsa cike da kwalla. Sannan ya kashe wayar, so yake Muhseen ya zo ya duba kamin aje da ita waje, domin ya san Muhseen ya kware a wannan bangaren. Taso yai daga saman kujerar ya dagota ya rumgumeta a kirjinsa sai ta lumshe ido ta sauke wani irin ajiyar zuciya. “I love you so much” Ya fada mata hawaye na sauko daga idonta suna sauka saman kanta. “Za ki warke Rahma In-Sha-Allah, zaki ji sauki ki tashi mu koma gida mu yi rayuwa tare da Ataa In-Sha-Allah” Shine abunda ya fada mata a hankali yana kara hugging dinta tightly. A asibitin yai isha'i sannan ya dawo dakin ya zauna, shi ya taimaka mata ita ma tai sallah, misalin nine Momy ta zo tare da abincin da Siyama ta duba jikinta ta mata fatan sauki sannan suia tafi. Aliyu kan a asibitin ya kwana rike da hannun matarsa, sallah asuba ce kaiwa ta fitar da shi daga dakin ita yana gamawa ya dawo. A nan ma shi ya taimaka mata tai sallah, sai dai yadda jikinta yai sanyi ya bashi tsoro sosai. Da kanshi ya hada mata tea da ruwan zafin daya gani a filas da ya kai mata tea a baki sai ta ki sha ta kawar da kanta. “Ba kya so ne?” Bata ce masa komai ba tana ta kallonta duk inda yai, hakan yasa ya dawo ya zauna ya rike hannunta, sai kuma ya koma saman gadon ya zauna ya dora kanta saman jikinsa ya rike hannunta yatsunsa cikin nata sai ta jinke yatsun nasa ta rumtse ido. Da dayan hannunsa ya karba wayar da Nasir ke masa sannan ya amsa ta Momy da Mama Fulani da kuma Daddy kamin ya kira Muhseen, jin number sa ba ta shiga yasa yai tunanin wata kila yana cikin jirgi ne ko kuma ya kashe wayar ne. Number Mama Fulani ya kira ya tambaye ta idab Muhseen yana nan sai ta fada masa cewar tun da dare Muhseen ya fada mata zai je sokoto kuma ta ji lokacin da ya fita tun da safe. Kashe wayar Aliyu yai ya jinginar da kansa ya lumshe ido. Sai ga wata likita ta shigo hakan yasa ya sauka daga kan gadon amman Rahma ta ki sakin hannunsa har likitar ta saka mata oxygen ta saita numfashinsa da na'ura mao kwakwalwa, sannan ta fita, sai ya Aliyu ya dawo saman kujera ya zauna yana rike da hannun na Rahama, ya dauki lokaci a haka kamin ya maida hannunta gurin fuskarsa ya Lumashe ido, ya dauki awa daya a haka kamin ya ji hannun Rahma da ke jinke da na shi ya sake ya zamana shine kadai yake rike da hannunta. Da sauri ya dago ya kalleta sai jin karar tsayarwar numfashinta ya ji a computer da ke nuna tafiyar numfashinta. Girgiza ta ya fara yi da sauri a rike kuma a rude bakinsa har rawa yake. “Rahma Dear... ” Ya fada a lokaci daya, sai kuma ya sake ta da sauri ya nufi kofa kamin ya karasa Muhseen ya turo kofar dakin ya shigo. Da sauri Aliyu ya rike hannunsa sai kuma ya kasa ce masa komai sai wani numfashi yake sama saman kamar zai fice daga jikinsa gaba daya, kansa ya dora a kafadar Muhseen har sai da ya samu relief na few seconds sannan ya dago ya nuna masa Rahma. *Ina mata son rage kiba? Ina mazan da kiba ta hana su sukuni? Ina masu jikin yai kyau kamar na yarinya? Ina masu fama da kujera ko wani ta bo a fuska? Ina masu fama da hawan jini? Masu diabetic? Ag cera an gwada yayi an tantance ingancin babu shakku ko kadan. AG cera ya zo domin ya temaki garkuwan jiki da kuma lafiyar jiki. Sinadari ne wanda ze magance matsaloli da dama wadanda suke hana garkuwan jiki aiki yadda ya kamata ko kuma yake rusa garkuwan jikin ita kanta.* *Cututtukan zamani daban daban sun sa mutane gaba kuma magance su yana da wahala; irin ciwon Sugar, hawan jini, ciwon sanyin kashi, ciwon gabobi da sauran su. Haka ma cutukka irin wadanda suka shafi fatar jikin wadanda sun hada da kyasfi, pimples, takurewar fata, rakainuwar fata da kuma haske da kyallin fata duka ana shan AG cera kuma yana temakawa wajen magance illolin nan. Mutane masu fama da rashin karfin jiki wajen kwanciya da iyali da kuma mata masu fama da yawan ciwon mara lokacin al'ada ta karshen wata suma baa bar su a baya ba. A takaice dai AG Cera yana temakawa wajen magance cuttukka daban daban wadan ke damun mutum. Domin karin bayani ku tuntuni mu a wannan number +60167474649 ko kuma ku ziyarci shafin mu http://agnutritioninternational.com.* Da sauri Muhseen ya nufi inda Rahma take ya shiga dubata. Fita yai da sauri ya kira wasu likitocin suka shigo, sai ya ja hannun Aliyu ya fitar da shi waje, ya koma ciki shi da sauran likitocin biyu suka shiga bata taimakon gaggawa, amman ina rai yai halinsa mai abu ya karbi abarsa a lokacin da yake so kuma ya ga dama. Aliyu na tsaye wajen kofar dakin ya kasa zaune ya kasa tsaye, sai safa da marwa yake jikinsa na zafi, gumi sai karyo masa yake zuciyarsa na bugawa da mugun karfi har ya kasa daidai ta numfashinta. Yana ganin Muhseen ya fito ya nufo shi da sauri ya tsaya a gabansa sai kuma ya kasa tambayarsa tana raye ko a mace, saboda yana tsoron irin amsar da Muhseen zai ba shi, shi ma Muhseen din sai ya kasa ce masa komai, be taba jin tausayin dan'uwansa kamar yau ba, be taba fargabar fada masa wata magana kai tsaye ba sai yau, be taba jin cewar idan yana da ikon da zai ma Aliyu wani abu da zai saka farinciki ba irin yau, ji yake kamar ace ikon dawo da rai a hannunsa yake da ya dawo da ran Rahma saboda Aliyu. “Innalillahi wa'inna ilaihirraji'u” Shine abunda Aliyu ya furta ya risina a gurin ya dafe kansa, ya san Rahmarsa ta tafi kenan, domin da ace tana da rai Muhseen ba zai yi fargabar fada masa ba. Muhseen ma risinawa yai ya dafa shi “Aliyu” Sai kuma ya kasa cewa komai, a lokacin da Aliyu ya dago ya kalli shi sai hawaye Muhseen ya gani a fuskar Aliyu ga wani kadewa da idonsa sukai su kai ja sosai. “Allah be halicce kan Rahma ba, kuma be halicce Rahma dan kai ba, ba za a kara maka wa'adin mutuwarka ba idan lokaci yayi balle kuma a karawa Rahma dan ta rayu da kai, ka yi hakuri kuma kai hamdala ga wanda ya baka ita kuma a yanzu ya karbe ta” Aliyu ya gyada kai tare da hade wani abu daya tsaya masa a makoshi ya mike tsaye yana share hawayensa, yana kallon Muhseen sai ga fuskar Rahma a fuskarsa, a take rayuwar da kai a da ta fara dawo masa, iyakar kokarin da yai na kawar da kansa daga barin kallon Muhseen ya fara takawa yana jin kamar ba tafiya yake ba saboda nauyin da kafafuwansa sukai masa, hannunsa ya kai ya rika ginin gurin yana maida numfashi a hankali wani abun ya tsaya masa a zuciya ya tokare masa. Da sauri Muhseen ya rika shi ya bude wani dakin da ke kusa da su ya shiga dashi ya zaunar da shi saman kujera. A take Aliyu ya lumshe ido ya bude bakinsa saboda samun taimakon numfashi, know one can express yadda Aliyu yake ji saboda be taba losing wani important person a rayuwarsa ba kamar yau, mamanshi tana raye, Mama Fulani na raye Daddy da Abbah duka suna raye, yana rayuwa da Rahma and he pray for Ataa Allah ya ba shi, bayan tarin dukiya da lafiya da Allah ya bashi, ga kuma samun cikin Ataa Allah ya bashi Allah ya hada masa goma da ashiri na farinciki duk shi kadai, be taba jin yadda ake jin zafin rasa wani ba, be taba sanin haka zafin rashi yake ba, be taba jin zafin rasa wani abu ba sai yau. Muhseen ya fito da wayarsa ya kira Momy da Mama Fulani ya fada musu halin da ake ciki. Cikin firgici da rudewa mahaifiyar Rahma ta shiga dakin da Rahma take ciki, ba kuka take ba domin ihun da take ya wuce a kira shi da kuka sai dai hargagi da kuwa. “Innalillahi wa'inna ilaihirraji'u, na shiga uku na lalace Rahma ta tafi ta bar ni, La'ilaha illallahu” Ikram da wata gwaggonsu na rikonta amman ta kasa yin shiru sai ihu take, har da tsalle tana direwa kasa, kaico mai rai bakon duniya, yau Rahma ta tafi kamar bata taba wanzuwa a duniya ba. Babu mai iya bayyana yadda Aliyu da mahaifiyar Rahma suke ji sai wanda ya taba rasa uwa ko uba miji ko mata, saboda sune the most important abu a rayuwar ko wane dan'adam. Cikin wani irin karfi Mahaifiyar Rahma take wai ko zata tashi, amman ina mai rai ya aiko an tafi da abunsa, daman can aro aka ba kowa, kuma ranar tafiyar tana nan zuwa komai daren dadewa. Ji take kamar ace tana da ikon dawo mata da rai da ta dawo mata da shi, da ace kudi suna maganin mutuwa a yau da ta cire ko nawa ne an bawa Rahma ranta ta dawo su yi rayuwa kamar da, ina ma tana da yadda za tai Rahma ta sake rayuwa. Fitowa akai da ita daga cikin dakin Ikram da Gwaggonsu suna ta kuka, ga Rahma kwance kamar tai magana amman babu numfashi ta zama gawa. Kan kace kwabo kofar emergency ta cika da sisters din Rahma kowa sai kuka yake, ciki har da Momy da wasu yan'uwanta da ta dauko su rakota, ba mahaifiyar Rahma ce kadai abar tausayi ba har da yan'uwanta da Aliyu, domin kana kallonsu kasan suna cikin damuwa marar misaltuwa. Momy kan ciki ta wuce gurin Aliyu har lokacin yana nan zaune a dakin da Muhseen ya shiga da shi yana zaune baya kuka kuma ba hawaye idonsa sun yi ja sosai ga wani gumi da har yanzu be daina zubo masa ba. Momy na shigo Aliyu ya kalleta da sauri kuma ya mike tsaye kamar zai yi magana da ita sai kuma ya kasa cewa komai. Karaso tai kusa da shi tana hawaye tana kallonsa. Sai ya rikata ya zaunar da ita ya zauna kasa ya dora kansa a kan cinyarta, auna rashin Rahma yake a ma'auni mai nauyi amman idan ya hada da Momy sai yaji nauyinta ya koma kamar bashi, da Momy ce ta mutu a yau da be san iya halin da zai shiga ba. “Ka yi hakuri haka Allah ya so, haka yake a sadda ya so ga wanda ya zo babu wanda ya isa ya hana shi balle har ya tambaye shi dalilin yin haka, kai ma zaka mutu balle abunda ka mallaka ko ka aje” Be ce komai ba bayan Lumshe ido da yai yana ta hade yawu ko abunda yake jin ya tsaya masa zai tafi. Sai kusan sha daya na safe suka bar asibitin tare da gawar Rahma suka nufi gidan iyayenta da ita. Babu wanda zai ga gawar Rahma ya ayyana cewar ta mutu har sai idan an fada masa ko kuma ta taba ya tabbatar, mai rai bawan Allah iyakar iskancin dan'adam idan yana da rai ne daga lokacin da aka zare rai daga jikinsa ya zama gawa yan'uwan ne za su saffara shi har a kai shi masaukinsa na gaskiya. Kowa ya yaba karfin halin Aliyu na yi ma matarsa wanka kuma yai mata surura kamar yadda addini. “Allah ga Rahma nan, baiwar ka ce Allah yau ta dawo gareka aron ran da ka bata yau ka karbe abun ka ya Allah, Allah ina son matata ka sani, ita kuma tana so na, mun yi zaman aure da ita na shekaru tsabanin da muka samu atsakanina da ita na rashin jutuwa ko fada ko bacin rai da gangan ko cikin rashin sani Allah ka shaida na yafe mata, Allah kai ma ina rokon ka yafe mata, Allah jinyar da tai kasa ta zama sanadin tsira, Allah ka sadata mala'ikunka na Rahma ka sadata da Annabin Rahma, Allah ka hada ni da matata Aljanna” Wannan karon be iya rike kansa ba ya fashe da kuka sosai kamar mace, har sai da aka shigo aka fita da shi, hankalin kowa be kara tashi ba sai da aka fito da ita akai mata sallah aka dauki gawarta zuwa makabarta inda gidanta na gaskiya yake kuma gidan kowa. Muhseen ne rike da Aliyu har aka kai makabarta aka saka ta cikin kabarinta, wa zai iya fadar yadda cikin kabari yake? Babu iyakar abunda ido ya gani ko ya ji a duniya ne kawai, the first thing da aka saka bayan gawar Rahma itace sannan aka saka tukane sai haki da ciyayi ya biyo baya, haka aka lullube kabarinta da kasa sai aka tabbatar babu wata kusurwa da wani abun zai iya shiga sannan aka kewaye kabarin ana mata addu'ar neman Rahma. Sannan aka taso aka baro ta can ita kadai daga ita sai aikinta. Gida aka kawo ana karbar gaisuwar, Momy kuma ta bukaci Aliyu ya koma gida su a can su yi na su karbar gaisuwar. Har lokacin Mama Fulani da Nasir ba su iso ba saboda mota suka biyo ba su samu jirgin da zai taso yau. Aliyu na kusan shiga motarsa Ikram ta zo ta miko masa wata wasika, idonta yayi ja sosai. “Minene?” “Ita ta rubuta ta, a lokacin da ka kirata bata iya magana ta miko min, na tambayeta ta waye tai min alamu da kai zan bawa” Kallon takadar Aliyu ya rika yi na few minutes kamin ya kai hannu ya karba jikinsa na ta rawa. Sannan ya nufi motar ya shiga, Muhseen ne ke tukawa har suka isa gida sai taba takardar yake ya kasa budewa. A can gurin Momy ma an cika da mutane yan'uwan Daddyn da Momy, har Daddyn da kansa da wasu abokansa da suke kusa da kusa suna tare, har da yan'uwan Mama Fulani da suke yola wadanda suka zo ta jirgi. duk wanda ke gurin tausayin Aliyu yake, sai da magariba Mama Fulani ta iso ita da su Maryam da Ammy gaba daya gidan aka kwashe ba a baro kowa ba. After Sallah isha'i Aliyu ya shiga bangarensa da ke cikin gidan ya kulle kansa a cikin dakin ya bude takardar cike da fargaba ya fara karantawa. _Zaka karanta wasikar nan ne wata kila, bayan ba raina domin na san ba sakan cewa ina asibiti ba, da farko zan fara taya ka murnar samun haihuwa da kai, kuma nai maka godiya na rufa min asiri da kai da hakurin zama da ni na tsawon lokaci, ina jin a jiki kamar ba zan rayu ba wani lokaci ba, amman ina rokon yafiyarka kuma ka nema min yafiyar Ataa da yafiyar Momy da duk wani wanda ka san na taba alaka da shi, ka nuna min soyayyar gaskiya Aliyu ta hanyar yi min addu'a bayan raina, Allah ya hada fuskokin mu a aljanna. I love you so much ina maka fatar alheri a sabuwar rayuwar da ka fara da Ataa, na san ka nuna min so, amman ni yanzu tawa ta kare, ka yafe min Aliyu kuma ka yafe wa mahaifiyata so na ne ya saka ta aikata maka komai, ka yi hakuri na san kana so na amman babu wanda ya iya kaucewa mutuwa, tarin dukiya ko lafiya bata amfani mai ita ba matukar mutuwa ta kusance shi, ka yafe min Aliyu_ Fuskarsa shakaf da hawaye ya gama karanta wasikar. Kansa kamar zai bare idonsa ya kumburo kamar ba na shi ba. “Na yafe miki Rahma na yafe miki, Allah ma ya yafe miki” Ya furta sannan ya mike tsaye ya shiga bandaki ya wanke fuskarsa ya fito harabar ya memi Abbah, can gefe ya koma da shi ya karbi number Mai Martaba saboda yana son kiran Ataa ya nema ma Rahma yafiyarta. Dakinsa ya dawo sai da ya fara gaisawa da Mai Martaba sannan ya gabatar masa da bukatarsa, sannan ya kashe wayar bayan Mai martaba ya tabbatar masa da za a fada mata, after like thirty minutes aka kira shi da line orange na can nijar wata bakuwar number wacce ba ta Mai Martaba ba. Yana yin picking ya ji muryar Ataa kasa kasa kamar marar lafiya, sai da suka gaisa ya tambaye ta ko bata jindadi ne ta fada mishi lafiyarta kalau. “Ya jikin Rahma?” “Babyna jiki da sauki sosai ta ce a fada miki tana gaishe ki kuma na nema mata lafiyarki, tsabanin da kuka samu a baya” Aliyu yayi kokari wajen ganin yayi magana da ita normal ba tare da muryarsa ta canja kuma ba tare da nuna akwai damuwa a tare da shi ba, sai dai kana jin muryar kasan baya cikin walwala. A maimakon Ataa ta tace ta yafe mata sai kawai ta fashe da wani kuka da cikin wayar har Aliyu ya kasa saurare ya kara wayar a kirjinsa yana hawaye. Mutuwa....! 💔 Allah kai mana kyakkyawan karshe, Allah ka jikan Babana da Rahma😭😭😭😭💔 *AG cera ya zo domin ya temaki garkuwan jiki da kuma lafiyar jiki. Sinadari ne wanda ze magance matsaloli da dama wadanda suke hana garkuwan jiki aiki yadda ya kamata ko kuma yake rusa garkuwan jikin ita kanta. Cututtukan zamani daban daban sun sa mutane gaba kuma magance su yana da wahala; irin ciwon Sugar, hawan jini, ciwon sanyin kashi, ciwon gabobi da sauran su. Haka ma cutukka irin wadanda suka shafi fatar jikin wadanda sun hada da kyasfi, pimples, takurewar fata, rakainuwar fata da kuma haske da kyallin fata duka ana shan AG cera kuma yana temakawa wajen magance illolin nan. Mutane masu fama da rashin karfin jiki wajen kwanciya da iyali da kuma mata masu fama da yawan ciwon mara lokacin al'ada ta karshen wata suma baa bar su a baya ba. A takaice dai AG Cera yana temakawa wajen magance cuttukka daban daban wadan ke damun mutum. Domin karin bayani ku tuntuni mu a wannan number +60167474649 ko kuma ku ziyarci shafin mu http://agnutritioninternational.com.* Kuka na ke sosai jikina na raya min cewar Rahma ta rasu daman tun a lokacin da ya tafi na ke jin ba dadi, yanayin yadda na ji muryarsa ma na san ba lafiya ba, domin alamu ya nuna ba ya cikin walwala duk dai ban san ainahin abunda yake damunsa ba, sai dai jin cewar Rahma na neman yafiyata na san mutuwa ce kadai zata saka ta neman yafiyata, idan kuma ba haka ba, wata kila kuma Aliyun ne ya nema mata da kansa saboda ta mutu. “Babyna kukan ya isa haka” “Hamma ba a boyon mutuwa, idan ma ta mutu da gaske ba zan iya dawowa da ita ba, kuka ba ya dawo da wanda aka rasa, da yana dawowa da ya dawo min da Babana da Lukman, amman duka na rasa su kuma kuka da bakinciki be dawo da su ba, zan yi kuka saboda tausayinta ne da kuma kai” “Bana son kukan ko tunanin ya janyo miki wata matsala, ke kadai kika rage min a yanzu sai abunda yake cikinki, idan na kara wani rashi ban san ya zan yi ba, rashi akwai ciwo sosai gashi ba zaka iya dawowa da wanda ka rasa din ba, akwai ciwo sosai ka rasa wani abun da kake so a lokacin da kake tsananin bukatarsa, akwai ciwo rabuwa da abokin rayuwa da ka shirya yin rayuwa da shi” Hannu na kai na share hawayen fuskata, na san yadda Hamma yake ji saboda be taba rasa kowa ba a rayuwarsa sai yau, mahaifiyarsa mahaifinsa duka suna raye, wani karin gatan ma sai Allah ya kara masa da Mama Fulani da Abbah duk shi kadai, ni ko na san zafin rashi saboda na rasa mahaifina da dan'uwana kuma na san zafin babu saboda ana tashi a cikin babu din, shi ko be san babu ba sai akwai kuma be san zafin rasa komai ba a rayuwarsa sai yanzu. “Fada min kina nan lafiya kalau” “Lafiyata kalau, kuma na yafe mata abunda tai min wanda na sani da wanda ban sani ba, Allah ya jikanta yai mata Rahma” “Amin na gode, cikinji fa yana lafiya?” “Komai lafiya kalau, zan fadawa Mama yanzu” “Okay ki kula min da kanki pls” Na gyada kai kamar yana gabana sannan na aje wayar akan gadon na zauna bakin gadon ina ta kuka, ban taba tsammanin jin labarin mutuwar Rahma zai sakani shiga damuwa ba balle har nai kuka, amman sai ga ni ina kuka kamar wacce na rayu da ita na tsawon lokaci na shaku da ita, a yau duk wata kiyayya da kishi da jin haushi ta kare, mai rabawa ta raba. Kaico mai rai ba abakin komai yake ba, lokaci daya idan Allah ya so kama ka sai ka raina kanka har makiyinka ya tausaya maka. Sai da na ci kuka na koshi sannan na fito falon Hajiya wato kakana idona a kumbure da kuma sauran hawaye na nufi inda Hajiyar take zaune na mika mata wayarta wacce ta ara min na kira Hamma da ita. “Lafiya kike ko?” “Rahma ce ta rasu” “Wace Rahma?” “Matar Hamma” “Innalillahi wa'inna ilaihirraji'u” Shine abunda ya fito daga bakin Mama tana dafe da kirji, na san ta ji mutuwar kamar yadda na ji, abun kamar daga sama kuma babu dadi ko kadan. A nan suka shiga tambayar wacece ita, Mama ce ta fada musu ni kan sai wani sabon kukan ya kubuce min, har ga Allah ban jidadin mutuwarta ba, dan tsabanin da muka taba samu da ita sai ya dawo min sabo ina ta ganinta a fuskata. A cikin dare aka fadawa Mai Martaba halin da ake ciki na mutuwar Rahma, a waya ya kira Daddyn Rahma yai masa gaisuwa da kuma Abbah da sai aka sadashi da Daddyn Hamma shi ma yai masa gaisuwa sannan yai ma Hamma din, mu kuma aka ce mu shirya domin zuwa gaisuwa, a daren ban yi banchin kirki ba saboda tunanin Rahma ina ta ganin kamar ba da gaske ne ba, sosai na ji mutuwarta kamar wani ginshike nawa na rasa, har na soma jin ciwon kai na kama ni, da safe sai ga ni da mura, tun da nai sallah ban koma ba bachin ba, saboda tunani ashe Allah be yi zamu zauna a guri daya ba, balle ma na ga kishinta domin ni dai bana jin ina da kishin ma amman na san nata na musamman ne a yanayinta da yadda na karanci halinta.   Ko da goma tai dukan mu muna airport, wani abu sai kudi, babu zancen siya mana tickets na zuwa Nigeria, da jirgin Mai Martaba muka tafi, ni, Mama sai kuma wasu cousins dinta mata biyu, maza biyu wadanda Mai Martaba ya turo su walkice shi su yi masa gaisuwar. Mun sauka sokoto cikin lokaci wani abun burgewa muna sauka motocin da za su dauke mu suka iso, a wani gidan suka so su kai mu mu huta kamin muje gaisuwar sai Mama da kanta ta ce a sauke gidan Momy su kuma Mazan sai su tafi can din su huta, haka kuwa akai ni da ita da wasu yayyunta mata aka sauke mu gurin Momy su kuma mazan aka wuce da su. Mun tarardar gidan da taro sai dai ba taro irin nan farinciki da walwala ba, domin kana kallon fuskarta duk wanda ke gurin kasan ba taron jindadi ne ya tara su ba. A cikin gidan kuma mata yan karbar gaisuwa, ganin taron ya karya min guiwa na san nima wata rana haka za'ayi nawa, ayi na kowa.   Husna da Siyam su kai mana lale marhabun duk da kasancewar suma basa cikin walwala sosai sai dai sun yi murna da ganina suna ta dauki ba kuma murna na marmari na kawai ba har da murnar cikin da na ke da shi. Mama Fulani kan ba wani sakewa sumi sumi da ita kamar ta Allah, Ammy da duka yaranta suna nan, har ma da su Maryam da Rukaiya duka suna nan. Kar ka so ganin yadda Momy taks ta kokarin dawainiya da ni, sai kace wata mai tsoron ciki ko kuma wacce bata iya komai, abinci ma idan za a kawo min sai an tambayi wanne na ke so gudun kar a kawo min mai saka ni tashin zuciya. A ranar kawunai na da Mama suka koma da kuma cousins din da suka rako Mama, bayan sun yi gaisuwar a can bangarensu Iyayen Rahma, ban za ci Mama zata iya zuwa tai gaisuwar rasuwar Rahma ba, sai gashi ta maida komai ba komai ba, kana kallon mahaifiyarta zaka san a firgice take, irin figirtar nan na rasa wanda kake so a lokacin da ba kai tsammani ba, mahaifinta kan ya sha jinin jikinsa kamar ba shi ba, sai kallona suke ta yi daga shi har Mommyn Rahma.   Bayan mun dawo daga gaisuwar ne su suka kama hanya, ni kuma aka bar ni nan a gurin Momy wai sai an gama karbar gaisuwa. Ina zaune saman carpet ni kadai a dakin ina salatin Annabina na ji shigowar mutum, ban waiga ba amman na san ko wanene tun daga kan kamshin turarensa, ta kuma yadda yake takowa zuwa inda na ke a hankali har ya iso. Ji nai an rumgume ni ta baya, sai na sauke ajiyar zuciya a hankali ni kaina na san na yi marmarin Hamma sosai tun a lokacin da na zo garin nan idona suke kai kayin ganinsa, amman ban saka shi a idona ba ko gaisuwar da su Mama da yan'uwanta suka masa ina kyautata zaton sai indai a can gidansa suka same shi ko kuma ya shigo ni ban ganshi ba ya fita domin tun shigowata gidan ban ji ko alamun motsinsa ba sai yanzu. Gafen kumatuna ya sumbata. “Fada min kina nan lafiya?” “Lafiya kalau, tun dazun muka zo amman ban ganka ba” “Ina ta kokarin boye kaina dan kar na yi arba dake har sai idan ke kadai ce, saboda ina mararin na rumgume ki na jiki a jikina kuma ba zan iya haka abun a agaban mutane ba” Ya fada ba tare da ya sake ni daga rumgumar da yai min ba. “Mama ta tafi” “Na sani na gode da ta bar min ke” Mun dauki lokaci a haka yana rumgume da ni ta baya, sannan ya sake ni ya mike tsaye ya zauna bakin gadon Momy, juyowa nai na kalleshi sai wani irin kaunarsa da tausayinsa suka dirar min a zuciya lokaci daya, ya rame sosai kamar ba shi na har idonsa sun fada kamar marar lafiya. “Hamma baka cin abinci?” Kallona kawai yake ba tare da yace komai ba. “Bari na saka Husna ko wata ta hada maka wani abu ko kuma idan akwai fura ka sha idan baka son abu mai nauyi” Ina mikewa tsaye sai ya riko hannuna ya dawo da ni kusa da shi ya zaunar ya ja ni zuwa kirjinsa ya rungume ya lumshe ido, ina jin yadda zuciyarsa take bugawa da sauri. “Na gode Allah da be dauke min Rahma ba sai da ya ba ni ke, kuma yai min tukuici da wani dan ko ya, ni kada na san halin da na ke ciki kuma ni kadai na san iya abunda na ke ji a zuciyata” Ya fada yana kara matseni a kirjinsa, rashi akwai ciwo sosai na san irin yadda Hamma yake ji a yanzu saboda ni ma na taba rasawa ba ma sau daya ba. Sai da ya ji kamar muryar wata a kusa da kofar dakin sannan yai saurin sakina ni kuma na mike tsaye cikin tsoron kar wacce ke maganar ta shigo ta gan mu a tare. Wata kanwar Momy ce ta shigo dakin da sallama ni na amsa mata sai ta miko min kofin fura. “Ga shi inji Yaya ta ce ki sha” “Na gode” Na fada bayan na saka hannu biyu na karba, sannan ta juya ta fice. Zaunawa nai kusa da Hamma na mika masa furar wacce aka damata da kirdirmon nono. “Ka sha” Ba min musu ba, ya karba ya sha sai dai ba da yawa ba, ya mikon min sauran. “Shanye” Na sha rabin kofin sai na aje ina ta kallonsa, gaba daya ya koma kamar ba shi ba, so silent fuskarsa ma abun tausayi kallo daya zaka masa kasan cewar mutuwar Rahma ta taba shi ba kadan ba, ni ma da ban saba da ita ba ta taba na shiga damuwa kuma nai kuka balle kuma shi da yake mijinta kuma su kai rayuwa da ita. “Ina auna yadda kika rasa babanki da dan'uwanki ne, kuma ki kaita dawainiya da mahaifiyarki, gaskiya Ayusher kin yi kokari kuma ke jajirtacciya ce, wani lokacin ana jarraba bawa saboda a gwada imaninsa da kuma irin hakurin da zai yi, ban yi tsammanin tunanin Rahma zai addabe ni kamar haka ba bayan rayuwarta, amman idan na tuna ki da abunda yake cikinki sai na jidadi kuma nai ma Allah godiya” Ya fada a hankali yana ta kallona da murmushi a fuskarsa sai dai ba murmushin farinciki ciki ko na jindadi ba irin murmushin nan na godiya ga Allah da kuma jin zafin wani abun a lokaci daya. Shigowar Momy ce tasa na dan ja baya shi kuma ya mike tsaye yana saka hannayensa aljihu ya fice, ni da Momy da kallo muka bi shi har ya fice sannan Momy ta karaso cikin dakin ta dauki kofin furar da ta aiko min tana dubawa. “Ba ki shanye ba?” “Eh na sha rabi” “Ki daina barin kanki da yunwa, na san ba za ki iya cin abu mai nauyi ba wata kila shiyasa na tanadar miki da furar” “To Momy” “Zauna” Ta nuna min kujerar da ke facing din gandon, bayan na zauna sannan ita kuma ta zauna bakin gadon. “Ataa ki matar aure ce a yanzu ina fatar kin san da haka?” Na gyada masa kai ina maida idona kasa. “Ke yarinya ce na sani, amman daga lokacin da kikai aure zancen yarinta ya kare sai dai a kira ki yarinya saboda shekaru ko kuma wani abun da za ki na shirme ko rashin tunani, ballantana yanzu da kike dauke da juna biyu” Na kasa yin kasa da kaina saboda kunya. “Mijinki na bukatar kulawarki a yanzu fiye da ko yaushe, na san ba ki san wata dawainiyar ba, amman kula da abincinsa ya ci ko be ci ba yana wuyanki a yanzu, karki zamana shi kadai zai dinga damuwa da ke, mijinko ya rasa daya abokiyar rayuwarsa hakan kuma ba karamin jefa shi yai a matsala ba, sai da taimakonki zai iya dawowa dai da ya manta komai kamar be faru ba, ki shimfida masa kalar rayuwar da kike son yai kuka ya bi saboda yana tsananin son ki ni na sani, na san ke ma kuma kin san da haka, ki rika yi masa abunda zai kwantar masa da hankali da saka shi natsuwa, hakan ba karamin kara mishi son ki zai yi, a yadda yake damuwa da ke kuma yake son ki idan kina nuna masa damuwarki akan rashin cin abincinsa zai ci saboda gudun damuwarki kuma zai sa ya rage damuwar, tun da akai mutuwar bana jin ya saka wani abu a cikinsa har yau sai ruwa, sannan ki rika yi ma mijinki addu'a a duk sallah musamman a sujadar karshe da kuma bayan tahiya kamin ki sallame, mace mai aure ma ba akarbar addu'arta har sai idan tana yi ma mijinta da kuma iyayenta” “In-Sha-Allah Momy” “Kuma ke ma ki kula da kanki, wani abun ba sai ance ki yi ba, ya kamata ace kin san aure kike a yanzu, kuma ke ce kadai a gurin mijinki, mijinki na bukatarki a yanzu fiye da ko yaushe, ina fada miki wannan ne saboda na san zaki iya kuma ke kadai na ke da tabbacin za ki saka shi cikin walwala a yanzu, mijinki be iya so ba, be iya ki ba, ba kuma iya sakawa rai abu ba, idan yana so gaba daya yake so baya ganin aibun abun har sai yayi zurfi a ciki, idan kuma ya tsane abu gaba daya yake tsanarsa baya iya ganin kyaun abu har sai yayi nisa a tsanarsa, idan kuma ya sakawa rai abu yana sakawa sosai ta yadda rashin abun nan zai yi ta damunsa yana cinsa a rai, daga ke har shi ni duk kallon yara na ke muku wani abu dole sai an nuna muku, saboda mun fi ku tunani da hangen nesa, na san ba ki yawance a komai ba, sai dai ke din jajirtacciya ce saboda gwargwarmayar rayuwa da kika sha, da kurciyarki kin fuskanci kalubale kala kala na rayuwa kamin yanzu, kuma da Allah ya tashi miki sakamako sai yai miki duka a lokacin da kike bukatar hakan, hakuri yana da kyau kuma yana da riba sosai duk wanda yai hakuri be ga riba ba to kadan yayi” Sosai na jidadin magangannun Momy, a natse ta fada amin komai kuma na fahimci manufar da nufi, daga lokacin na sakawa kaina zan iya, kuma na fara jina a matsayin mace mai aure mai daraja wacce zata iya kula gidanta da mijinta da kuma yayanta duk kuwa da irin karancin shekaruna. Idan na waiwaya baya kadan na tuna abunda ya faru da ni irin halin rayuwar da muka shiga da fadi tashi da nai sai na ga wacan rayuwar kamar labari aka ba ni ba ni ce na wanzu a cikinta ba. “Tashi ki bi mijinki ku kwana a can” Maganar Momy ta katse min tunanin da nake. “Ba ki bukatar komai dai ko?” “Babu” Na fada ina mikewa tsaye na dauki Hijabina na saka, sannan na fara takawa a hankali har na fito falo. “Matar yaya ina za ki je?” Siyama ta tambaya tana kallona da murmushi a fuskarta. “Gida zamu je” “Ba anan za ku kwana ba?” “Eh” Na amsa mata muryarta da kamar damuwa. Sannan na karasa kusa da Mama Fulani na dan risina na ce mata. “Mama za mu tafi gida sai gobe” “To Allah ya tsare” Ya mayar min tana kallona, sannan na karasa gurin Ammy ita ma nai mata sallama da wasu kannen Momy da yan'uwan Daddy sannan ya fito harabar gidan. Na yi mamakin ganin Muhseen tsaye jikin motar Hamma yana magana da shi, ban san mi yake fada masa ba na ga dai Hamma ya gyada kai sannan ya bude min gaban motar tun kan na karaso. “Ataa” Kiran da Siyama tai min ne yasa na juyo sai ta nufo ni da yar karamar dogowar kular silba a hannunta. “Ga shi wai Momy ta ce ku tafi da shi” “Mun gode” Na fada bayan na karba, ko da na juyo ban ga Muhseen ba balle mafarinsa sai Hamma tsaye yana ta kallona har na karasa, hannu ya kai ya karbi kular hannuna sannan ya matsa daga jikin motar wanda hakan ya bani damar shiga ciki na zauna shi kuma ya rufe motar, ya zagaya bangarensa ya shiga yai ma motar key.   A hanya ya rika tambaya ko ina son wani abu, sai na ce masa bana bukatar komai, amman duk da haka sai da ya tsaya ya siya min gassashiyar kaza da yoghurt. “Bana jin yunwa fa” “Za ki iya bukata da dare ai, kuma ba dan ke kadai na siya ba” “Dan wa?” “Babyna” Ya fada min fuskarsa babu walwala. Har muka isa gida ban sake ce masa komai ba shi ma kuma be ce min ba, har sai da ya faka motar na kai hannu zan bude. “Tsaya ba ri na bude miki” Fita yai ya zagayo gefena ya bude min motar na fito sannan ya rufe, ina gaba yana bayana har muka shiga cikin falon, sai ya zauna saman cushion yana ta kallona. “Na hada maka ruwan wanka?” “Zo nan” Zuwa nai na zauna saman kafafuwansa kamar yadda na bukata sai ya rumgume yana sauke ajiyar zuciya a hankali sai dai hakan be hana ni jin saukarta. Mun dade a haka kamin ya barni na daga jikinsa mu shiga daki, rumguma a cikin abunda Hamma ya ke so kuma ni ma nake so domin ina jin natsuwa sosai idan ya rumgume ni hakan kuma yana kara min jin son kusanci da shi sosai. Cikin jikinsa na kwana kamar kullum sa'a daya nai ban farka cin abincin dare kamar yadda na saba ba. A lokacin da muka gama sallah asuba kuma sai na nufi kitchen na bar a dakin yana karatun qur'ane ni kuma na shiga na kunna gas din na sarrafa dan abunda na iya na ruwan zafin tea da suya wainar kwai da dankali sai kuma doya, sannan na bude kular da Momy ta ba mu jiya, farfesun kayan ciki ne a ciki, sai kawai na dora su akan wuta na dumama na juye a wata kular. “Wow da kanki kike girki, na fada miki bana son wahalar nan da kike miyasa ba ki jin magana” “Dan na yi aiki ba komai cikin zai yi ba, kuma ni bana son abincin waje” “To amman sai ki bari idan na gama karatu Quranen na hada ko?” “Bana son girki na namiji” Wannan karon yayi kokarin fadada  fuskarsa da abunda ya rasa daga lokacin da akai mutuwar nan zuwa yau wato murmushi shi ma kadan. “Kin taba jin inda da zai ce baya son abincin babansa” “Haka dai yace wai babansa be iya girki ba, idan ma yayi babu dadi shiyasa nake turo min shi nai amai” Na fada ina yatsina fuska, sai ya kara matsowa kusa da ni ya rika hannayena. “Karki masa karya, na san ba zai ce haka ba, ta ina ma kika ji ya ce haka? Yaushe kika iya karya” “Yanzu” Na fada da kamar kunya, sai yai murmushim gefen fuska yana aje numfashi. Shi ya taimaka min na karasa hada komai, sannan muka karya, be wani ci da yawa ba shi ma kuma dan na matsa masa ne, ni kan na ci abincin sosai kamar wacce ta kwana da yunwa, ni kaina har mamakin yadda na ke cin abinci sosai na ke kamar ba cin lafiya ba. ***  ***   *** Har akai zaman makokin aka gama Mommyn Rahma bata koma normal yadda take ba, damuwa ta taru a ranta ta tsaya mata, ba ita kadai ba gaba daya gidan babu wanda mutuwar Rahma bata taba shi ba, yau duk wani abu da Rahma ta mallaka na jindadi da dangi da kaunar iyaye da miji yau ta tafi ta barsu, mutuwa ta ishi kowa wa'azi, yau iyayenta sun ga Abunda kudi ko iko ko milki ko isa basa badawa wato rayuwa, komai ikon ka da isarka da milkinka baka isa ka hana mutuwa daukarka ba, kamin mutuwarta sun ga abunda ya kamata yace ya zame musu ishara, na juyarwar al'amarin da ba su taba zaton zai zame musu haka ba, duk wani abu da Daddyn Rahma ko mahaifiyarta ko ma ita Rahma da kanta take takama da shi na familyn Ataa ne yarinyar da suka wulakanta suka maida ba komai ba, a karkashin inuwar kakanta suke takama ta gidansu ce, ita din da suke gani ba komai ba Allah ya mayarda ita saman su, wani karin bakinciki ma ta zama ita kadai a gidan Aliyu babu yarsu a gidan balle tai kishi da ita. Yau sun koma sune kasa ta ko wane bangare. Sai da akai aka gama karbar gaisuwa sannan Mama Fulani da Ammy suka koma Abuja tare da Abbah daman shi Muhseen kwana biyu kawai yai ya koma saboda yanayin aikinsa. Nasir ma da matarsa sai da suka kara kwana daya saboda Aliyu sannan suka wuce. Aliyu da kansa ya raka su har airport lokacin da za su tafi, Nasir yayi ta bashi hakuri da kuma kalaman da za su karfafa masa guiwa su akan rashin Rahma.   After ya raka su ya dawo gidan Momy duk ya zama wani silent kamar ba shi ba, lokaci lokaci Rahma take fado masa a rai, idan ya tuna cewar be cutar da ita a zamantakewar su da aure ba sai ransa yai fari tas domin babban abunda yake gudu a rayuwarsa zalintar wani ko danne masa hakki da ikonsa, and wani abun godiya ga Allah da Allah ya saka ba Ataa ce ya rasa a yanzu ba, domin da ita ta tafi a yanzu maimakon Rahma wata kila da zai fi shiga damuwa sosai fiye da Mutuwar Rahma, duk wani abu da yake game da Rahma sabo ne kawai da kuma tuna irin rayuwar da akai ko makinyin ka ne ya rasu sai ka ji babu dadi balle kuma matarka, yana yawan ayyanawa kansa wata rana zai mutu Rahma ma zata mutu saboda matsalarta tun daga kan cire mata koda da akai na farko da ta biyun ta lalace aka canjin mata wata da ta mahaifiyar Ataa ta zo ta kone abun ya soma ba shi tsoro. Wata kila ta kone ne saboda Allah ya nuna musu ikonsa akan abunda suka aikata sai dai hakan be zame ma Rahma da iyayenta ishara sai ma kokarin aikata wani suke, yanzu kuma da mahaifiyarta zata bata nata sai Allah ya gwada musu ikonsa ya karbe abarsa a lokacin da suke tsananin bukatarta kuma babu yadda suka iya da ikon Allah. Yar da suke kishi da fada akanta mai abu ya karbi abarsa kuma ya maida wacce suke kishin da ita asaman su sai kuma ya? ATAA POV. kamar yadda Momy ta fada min ina kokarin ganin Hamma ya ci abinci ko da ba da yawa ba, kamar yadda ni ma yake tsare ni na tisani a gaba dole sai na ci na koshi a cikin satin sai ya zama ni da shi muna bawa junanmu kuwawa ta musamman da kuma ganin tausayin junanmu, yana ganin tausayin cikin da na ke dauke da shi da kuma tausayi Rahma sai ya dawo kaina ni kadai daman can kuma ga kaunata a ransa, yadda yake tallalina kana ganin abunda yake min kamar mai tsoron ya rasa ni ne, ni kuma tausayinsa ya cika raina sosai na rashin Rahma da yai da kuma yadda baya iya bawa kansa kulawa ta musamman amman yana kokarin kula da ni. Wanda ya rasu shi ya tafi babu abunda za a canja daga rayuwar wani ko kuma duniya gaba daya, daga lokacin da rayuwarka ta yanke shikenan kai na manta da ka taba wanzuwa a wata duniyar ma, kana ciki kabarinka kana fuskarta abunda ka aikata idan alheri ka fara gani idan kuma akasin hakan ne shi ma zaka gani. Na karu da abubuwa da dama a mutuwar Rahma a ciki akwai na tunatar da ni cewar saboda na samu jindadi da kwanaciyar hankali a yanzu ba shi yake nufin mutuwa ta manta da ni ko kuma ni na manta da ita. Abu na biyu kuma na yarda wanda ya mutu shi ya mutu duk kuwa irin son da ake masa, domin Hamma ya dan fara sakewa ba kamar da ba, daman kuma ai ba zai dawwama a cikin bakincikin mutuwarta ba kamar yadda take tsammani saboda Allah ya musanya masa da ni, wata kila da ace ta tafi a lokacin da be aure ni da zai fi shiga damuwa sosai, a kokarinsa na faranta da saka ni nishadi ni da abunda yake cikima kamar yadda yake fada, sai shi ma ya saka kansa ba tare da ya sani ba, ban ayyanawa a raina cewar wata rana Hamma zai so ni kamar haka ba, kuma zan rayu a gidansa daga ni sai shi sa abunda zan haifa inda da rai da rabo.   Kusan kullum ina waya da Nana wacce na ke kira da Mama a yanzu saboda canjin da Hamma yai min tama tambayar lafiyata da ta Hamma na fada mata muna nan lafiya, har take fada min akwai yan'uwa da yawa da ban gani ba sai idan komai ya laba na dawo, ni dai sai dai na amsa da to amman na san yadda Hamma yake daukin cikin nan da ni ba zai iya barin nai nisa da shi ba, idan muna gida a jikinsa na ke wuni idan kuma mum taho gurin Momy idonsa na kaina da na yi wani abun da ba daidai ba sai yi kin alama da ido. Momy ma tana kula da ni har zaman da ke kusa da kofa sai ta fada min wai mai ciko bata zama a bakin kofar dakin ko kusa da kofa aaboda aljanu, ni dai abun har dariya ya ba ni sai dai ban yi a gabanta ba, ni dai ban taba jin haka ba wata kila saboda ban zauna da tsofi ba ko kuma ban yawance akan irin waennan abubuwa, wata kila kuma saboda suna son cikin ne suke ganin komai be dace nai yi ba. Shi kanshi Hamma da safe sai ya min addu'a har a cikin haka ma da dare idan zan kwanta. A ranar da muka wuni idan Momy take masa maganar karatuna sai ya nuna mata baya so. “Momy ga ciki kuma ace tai karatu? Haba abun ai sai yai dawo, da karatunta zan ji ko cikin?” “Wai dan wajen Fulani kanka farau ciki ne? Karatu ko na islamiya sai ta fara da shi a yanzu, saboda kula da kanta da addu'oi, ai ilmin mace yana da muhimmanci ba wai ko dan aiki ba, saboda kula da yayanka ma ta koya mu su, kuma idan babu ilmi tarbiyar ma ya kake tunanin za ayi ta? Miyasa ake son auren mace mai ilmi ba dan wannan ba” “Momy ki ma kinsan dan wajen Fulani da Mama Fulani komai na su dabam ne, gaskiya ni ba zan iya daukar wannan ba, ke ma fa Momy kin san yadda ake bukatar abun nan yanzu kuma ki kawo wasu maganganu haba dai Momy” “Haba dai? Yanzu kana ganin idan a gurin Kakanta take kuma ya samu labarin bata iya komai ba batai karatu ba zai zuba mata ido haka? Yanzu ka fi son tai ta zaman banza a wata bakwai ko takwas da ke tafi wanda za tai nan gaba? Ai ya kamata ka saka ta ilslamiya ko kuma na nemo malamin da zai rika karantar da ita a gida, in so shi bokon idan ta haihu sai ta yi, baka sani ba ma ko tana da burin yin wani abu da karatunta” Momy na fadin hakan ni kuma nai karaf na ce. “Eh ina son nai likita ko nurse abun na burge ni sosai Wallahi” Harara ya watso min. “Eh ba ri ki sake magana na buge miki ba ki a nan, haka nan za ki je ki yi karatun likita shekara nawa tare da maza?” “Ai ansan ina da aure kuma zan rika saka hijab har da niqab ma” “Ba za ki yi shirun ba? Ba ki san kyaunki hadari ne ba, kuma ba ki da wayo da za ki iya tattalin abunki balle har ki kare martabarki, ni ko ko tafin kafarki aka kalla aka yaba Wallahi zafi zan ji” “Allah ya sauwake maka wannan bakin kishin daya cika maka zuciya, amman karatu kan dole ne tai yarinya ba za tai zama haka ba, kai ma da yarka ce ai ba zaka barta haka ba” “Momy za tai karatu, karatuna yana cikin burin da na ke da shi akan Ayusher amman sai ta haihu ta yaye abunda ta haifa ya yi kwari sannan a fara maganar karatun shi ma idan bata samu wani cikin ba” “Yanzu a maimakon zaman da za tai ai sai ka sakata ta fara daga matakin farko kamin ta haihu dan yai kwari ta san wani abu ka ga ci gaba kawai za tai” “Momy mun ma kusa barin garin nan Abuja za mu koma” “Ai a Abujar na ke nufin ka saka ta ba a nan ba, daman can sun fi makarantu masu kyau ai” Na jidadi sosai da Momy ta tunatar da shi burina da kuma abunda na ke ta mafarkin samu shekaru da yawa, domin na ga kamar shi ya manta idan ma be manta ba to yana son shashantar da abun saboda kar dansa ko yarsa su wahala. Ni ko ban ga abun wahala a ciki ba domin bana jin komai ko aman da nake na dade ban yi ba sai dai yawan cin abinci da na ke sosai kuma akai akai. “Shikenan Momy daman can na san ai ba ke ce Mama na ba, shiyasa ba ki goyon baya na, da Mama tana nan da yanzu ta saka baki ta tsaya min” “Daman can ai kai ba dan ba ne, balle kuma yanzu da na samu yata ta, ga su Husna da Amina da Siyama sun ishe ni ga kuma Muhseen a gafe” “Na kusa komawa gurin Mahaifiyarta na barki da su” “Ai da ma kabar ta nan ta yi karatu ta koyi abubuwa da yawa kamin nan” Dariya yai dan yana jin kamar ba da gaske Momy take ba, ni dai na yi yar dariya dan san Momy ta fada masa abunda ba zai iya ba ne. “Tashi mu je gida” Ya fada har lokacin be daina dariya ba, ita kanta Momy dariyar take dan ta san abunda ta fada ba mai yiyuwa ba ne a gurin Hamma. Muna shirin barin gidan kiran Wayar Mama ya shigo wayata da zumudi na daga na kara a kunne, ba ma kamar da ta fada min cewar gobe zata zo sai da n daka tsalle na dire saboda murna da yaren buzanci na ce. “Haka nan kawai za ki zo Mama?” “Aa saboda maganar likitan nan ne, gobe za a zauna da shi da ni da ke da wasu yan'uwana da Mai Martaba zai hado mu da su” “Daman maganar tana nan?” “Tana nan mana ai kinsan ba za a bari ba, tun kwana baya suka kira suna fadawa Mai Martaba suna son ganina da ke sai ya nemi a dan daga mana kafa saboda an yi ma mijinki rasuwa ni kuma bana ma kasar a yanzu” “Amman na jidadi Allah ya kawo ku lafiya Mama” “Amin sai mun iso” A haka muka rabu ina ta jindadi zan ga Mama daman na yi marmarinta saboda na sabu da ita ban ma dauka zan iya daukar tsawon lokaci kamar haka ba tare da ita a kusa da ni ba, kuma har hankali ya kwanta haka. “Mama ta ce tana nan zuwa gobe” “Na sani ai” Hamma ya fada abun sai ya bani mamaki sosai daman ya san da zancen zuwan be fada min. “Ya akai ka sani?” “Daddy ya fada min, kuma ina son ki ga Mama a ba zata ne shiyasa na kyale ban fada miki ba” Na yi murmushi, Momy kuma ta yi dariya tana kallonmu cike da burgewa. Na y zaton zai ji kunyar Momy ya bar ni na bude motar da kai sai gashi ya bude duk kuwa da kasancewar Momy na tsaye bakin kofar falo tana kallon mu, sai da na shiga sannan ya rufe yai mata key ya danna horn aka bude mana gate. Sai da muka fara tafiya sannan ya kama hannuna yana murzawa a hankali ba tare da ya kalleni ba. “Hamma....” “Babyna bana son Hamma nan” “To ai ance ba a fadar sunan miji” Murmushi yai ya kalleni sai ya kai hannun nawa a bakinsa yai min kiss. “Then fada wani suna mai dadi, not Hamma sunan ma dariya yake ba ni” “To me zan ce?” “Ki kirkiro da kanki mana” Na yi shiru ina ta nazarin sunanshi da zan bashi bayan Hamma da Aliyu. “Z a k i” Kyalkyalewa yai da dariya ya faka motarsa gefen titi ya riko fuskata yana kallona. “I love you so much Girl ke duk abunda zuciyarki ta nuna miki shi ne daidai” Na yi dariya, sai ya hada goshina da shi ya goga min hancinsa yana ta kallon cikin idona, hakan yasa na rumtse idon sai na ji lips dinsa saman nawa. Hakan yasa nai hanzarin bude ido sai yai min murmushi ya dauke bakinsa ya rike fuskata yana ta watsa da yatsansa a lips dina sai wani lumshe ido yake yana ta kallon bakin nawa yana hade yawu. “Wani suna mai dadi dai, ba Zaki ba wanda ba za ki ji kunyar kirana da shi a gaban kowa ba” “To amman ba yau ba sai na yi dogon tunani” Dariya yai ya shafi fuskata ya tashi motar, kamar kullum yau ma sai da ya biya ya siya mana kaza da yoghurt sannan muka isa gida. Sai da muka fara cin kazar sannan ya hada mana ruwan wanka muka shiga mukai tare. “Ni fa na fi jindadin yin wanka ni kadai” Na fada bayan mun fito ina daure da tawul kamar yadda shi ma yake. “Wanka tare yana kara soyayya da kauna da rashin kyamar juna, Annabi ma yana wanka da iyalansa, kuma duk abunda yai ko ya ce ayi yana da fa'ida sosai a garemu da falala, kuma yana yi saboda ya zame mana abun koyi sosai, ni kin ga yanzu na saba yi da ke idan ina yi ni kadai ma bana jin dadi” Dariya nai, na nufi gaban madubi ina gyara gashin kaina, sai ya zo bayana ya tsaya, yana kallona ta cikin madubi da cat eyes dinsa. “Gaskiya na yi dacen mata” Ya fada yana kai hannunsa ya shafa wuyana zuwa dantsen hannuna da yatsansa, wani yar na ji hakan yasa nai saurin juyowa, sai jin dariyarsa nai. “Ba ki da wayo, ai ta nan ta fi min sauki ma” Ya fada yana dauka ta cak ya nufi gadonsa da ni. *AG cera ya zo domin ya temaki garkuwan jiki da kuma lafiyar jiki. Sinadari ne wanda ze magance matsaloli da dama wadanda suke hana garkuwan jiki aiki yadda ya kamata ko kuma yake rusa garkuwan jikin ita kanta. Cututtukan zamani daban daban sun sa mutane gaba kuma magance su yana da wahala; irin ciwon Sugar, hawan jini, ciwon sanyin kashi, ciwon gabobi da sauran su. Haka ma cutukka irin wadanda suka shafi fatar jikin wadanda sun hada da kyasfi, pimples, takurewar fata, rakainuwar fata da kuma haske da kyallin fata duka ana shan AG cera kuma yana temakawa wajen magance illolin nan. Mutane masu fama da rashin karfin jiki wajen kwanciya da iyali da kuma mata masu fama da yawan ciwon mara lokacin al'ada ta karshen wata suma baa bar su a baya ba. A takaice dai AG Cera yana temakawa wajen magance cuttukka daban daban wadan ke damun mutum. Domin karin bayani ku tuntuni mu a wannan number +60167474649 ko kuma ku ziyarci shafin mu http://agnutritioninternational.com.* Na farka cike fa far'a da kuma farincikin zuwan da Mama za tai, ban taba tabbatar da na yi missing dinta sosai na sai da na farka da kewarta. Hamma ya shirya mana abun karyawa ni kuma na gyara gidan a wauta taa na zata gidan zata fara sauka sannan ta wuce gidan Momy. Bayan na gama komai muka zauna muna karyawa sai ga Momy ta kira Hamma a waya tana labarta masa cewar Mama ta zo tana gurinta. “Laa ba nan za ta sauka ba?” “Shikenan sai ta sauka nan saboda ga ta ita mai ya ko?” “Amman na dauka nan zata sauka, har ina shirye shirye girka mata wani abu” “To an hutar da ke” Ya fada yana jan hancina. Sai nai murmushi. “Ita ma zan mata magana na ce tai maka maganar karatuna” “Oh magana kika yi ma Momy tai min magana ko?” “Aa Wallahi ita tai dan kanta,kawai dai ina son karatun ne kuma kai na ga kamar ba ka so” “Ba wai so ne bana yi ba, yana ganin kamar karatun a yanzu zai iya zame miki matsala ko wahala” “Wallahi ba wani Wahala bana jin komai fa kalli” Na yafa ina daga rigar da ke jikina, sai ya kalli cikin ya kalleni yana murmushi. “Ai a jikinki ake gani ba, nan gaba na ke miki nuna” “Idan na ji da wahala nan gaba zan daina” “Daman ai kin iya raki ai” “Amman ni ai ina da kokari bana raki a komai ma” “Ko” Ya tambaya kamar mai magana da yar shekara uku babu dariya ko murmushi a tare da shi. “Idan mun koma Abuja zaki fara zuwa islamiyar su da bokon da ke can, amman idan cikin ya kai wani mataki za ki saurara da zuwan har sai kin haihu, sannan ki cigaba” Ban san lokacin da bar inda na ke zaune ba, na fada jikinsa ya rumgume shi ina murna. “Da gaske Hamma” “Ba na ce ki daina ce min Hamma ba?” Ya fada yana jan lips dina. “Ni dai amsa min da gaske?” Ya gyada kai sai na kara rumgume shi saboda murna har da yi masa kiss a gefen fuska, shi kansa abun sai da ya bashi dariya. A ranar sai farincikina ya zame uku, na zuwan Mama da na case din Doc Asim da za ayi ga kuma zancen Karatu da Hamma yai min. Kowa ya ganni a wannan lokacin ya san ina cikin farinciki, har muka yi wanka muka shirya ban daina sake saken yadda zan fara karatun nawa ba. Bakar a baya na saka shi kuma ya saka wani koren yadi mai kyau mai kamar boyal kuma ba boyal ba, ya saka bakar hula da bakaken takalmi karka so ganin mijina a wannan lokacin yayi kyau sosai fuskarsa har wani annuri take kamar wani ango, ni kaina sai da na kusa shashantar da kaina gurin kallonsa. “Ashe kai ma kana da kyau” Ya dube ni da duba irin na wasa da kuma mamaki. “Oh dacan ba ki taba ganin kyau na ba sai yau? Ko dan ina yawan fada miki cewar kina da kyau?” “Aa gaskiya yau dai sai naga kamar kana da kyau” Hannu ya kai ya rikoni ya matse min kunne. “Na fiki kyau yarinya ni da yan mata ke hari ma, ke ma ba kyau ne ya janyo ki ba, kina ga dan yaro kyakkyawa kika lake min har da addu'ar Allah yasa na so ki, shiyasa na kasa zaune na kasa tsaye sai da na kawo ki gidana” Ban san lokacin da dariya ta subuce min ba, duk kuwa da irin zafin rikon kunnen da yai min. “Da zafi sosai da zafi” Na fada a lokacin da yake jan kunne nawa zuwa gurin motarsa. “Yau ke za ki bude min motar na shiga” “Saboda me?” “Saboda ni ne Sarki” “Amman ai kai ka saba bude min” “Lokacin da kina sarauniya ba” “Yanzu fa” “Ni ne sarkin” “Taya?” “Gashi nan ke ma kin yaba kyau na” Dariya nai na daka tsalle na cire hular kansa na watsa da gudu gaban motar sai ya biyoni ya gudunsa. “Ke ba ki da kai ya za ki fara gudu da ciki” Jin hakan yasa na tsaya sai kawai ya karaso kusa da ni ya karbe hularsa ya sake rike min kunne. “Na gane ba ki jin magana Babyna” Haka ya janyo ni har gurin motarsa ya bude min na shiga ya rufe sannan ya zagayo ya shiga mazaunin direba ya tashi motar muka dauki hanyar gidan Momy. Ina shiga dakin Momy yai kan Mama da gudu na rumgumeta ina murna. Matan da ke tare da ita sai suka saka dariya suna ta kiran wai na cika kurciya, Momy ma dariya take tana fadin haka muke ni da Husna da Siyama kusan halin mu daya Amina ce kawai mai hankali, sai da muka dade a dakin muna fira ni har na manta da Hamma sai gashi ya shigo dakin da kunya ya gaishe su tare da musu fatar an zo lafiya sannan ya fita. Wani abun haushi abun mamaki Mama ta yi ma kowa tsaraba, a gidan sun daga kan Daddy har Momy da Amina Husna da Siyama kai har Hamma sai da ta siyo masa wata dakakkiyar shadda yar Agades amman ban da ni, nikan Nonon Ragumi ne kawai tai min tsaraba da shi. Misalin biyu saura na rana muka fito zuwa inda ake bukatar ganinmu, ni da Hamma a mota daya Mama kusa ta shiga wata mota da yan'uwanta maza suka zo da ita daga can inda suka sauka. Ko da muka isa gurin biyu daidai, wani katon gurine mai kamar ma'aikata, yan'uwan Mama maza da Hamma suka shiga gurin da aka tana da domin sallah, ni kuma da Mama da wata yar'uwarta da ake kira da Mama Lattu muka shiga wani dan fili mai kamar dakin karatu mukai na mu sallah. Ba mu zauna a dakin ba sai uku daidai domin bayan gama sallah sai da aka jira isowar wasu daga cikin wadanda za a zauna da su. Maza da mata ne da yawa a dakin za su kai su goma a dakin, sai wasu kujeru da aka jera can dabam wadanda aka nuna mata aka ce mu zauna, duk irin kusancina da Hamma na kasancewar mijina hana shi shiga akai a gurin, da kuma yan'uwan Mama sai aka hana su shiga, wai da mu kawai suke son su fara magana. Inda Doc Asim yake zaune da dabam da inda muke zaune, sai kallona yake kamar be tana ganina ba, na kalleni ya kalli Mama wata kila mamakin rayuwarta ya kashe shi ko kuma mamakin kawo kararsa yake oho, sai dai a yanayin da ya ganmu daga ni da har Mama ya sam yanzu ba kamar da ba ce domin ta canja zane. Da turanci suka fara magana kamin dayan ya fara yi da hausa yadda ni da Mama za mu fahimta. “Doc Asim ka san wannan?” Sai ya kalleni ya gyada kai. “Eh na santa” “A ina ka santa?” “Ta yi zaman jinya asibiti tare da mahaifiyarta a lokacin da ta siyar min da kodar mahaifiyarta” “Ke kin sanshi?” “Eh shine likitan da ya cire kodar mahaifiyata ba tare da sanina ba ko saninta” Daga haka suka fara karanto masa abunda ake kara akansa da kuma zarginsa da ake. “Wannan yarinyar fa karya take ita ta siyar da kodar mahaifiyarta, kuma ta kai karata a gurin police ba ta ci nasara ba suka koreta shine yanzu take kokarin ganin ta bata min suna, wasu ne suke sakata saboda aci min zarafi” Sai da suka tambayeni sannan na bayyana komai yadda ya faru ciki har da kulleni da akai gurin police, da suka tambayi ko ina da shaidu akan hakan sai na ce shukura ce ta san komai yadda ya faru. “Fine na yarda a nemo shukura za ta fadi gaskiya ai, and zan kawo takardar da ta saka hannu akai za ku ga komai” Yana fadar hakan na raya a zuciyata cewar akwai abunda yake kokarin shiryawa, wata kila ita ma zai siyeta kamar yadda yai ma polisawan da suka kama ni. “Za mu cigaba da bincike, za mu gone gaskiyar lamarin idan har ba shi da laifi za mu hukuntashi, kuma zamu mika shi kotu domin ta hanke masa hukunci daidai da abunda ya aikata, ba zamu yarda wani likita ya bata mana aiki ko suna ba, ko kuma ya taka daya daga cikin dokikinmu, idan kuma ke muka samu da laifi yin masa kazafi za mu hukunta ki babu ruwanmu da kasancewar jikan Sarkin Agadaz babu ruwanmu da kudin kakanki ko babanki za mu hukunta kuma mi mika ki kotu domin a yanke miki hukuncin daidai da abunda kika aikata” “Na yarda” Ina fadar hakan Doc Asim ya maida hankalina a gurina, wata kila yana mamakin yadda nake da karfin hali ne wata kila kuma yana mamakin jin alakata da wani babban mutum nw kamar sarkin Agadaz da kuma zancen kudi da sukai ko da be san waye shi ba yana ji ya san ba karamin mutum, a take yanayinsa ya canja ya koma kamar ba shi ba rama yai ko lalacewa ba, yana nan yadda yake amman hankalinsa ne a tashe, domin ya san waennan likitocin ba kamar police ba ne da zai iya siye su ba. Ninkaina a yadda na gansu na san za su adalci ko da yake abun ba a fuska ba ne, da a fuska ne da Doc Asim ba zai min haka ba. Dukanmu da farinciki muka dawo a mota na ke labartawa Hamma yadda akai yana ta kara kin kwarin guiwar cewar za su yi adalci domin gurin ba gurina na wasa ba, kuma ya san wasu daga cikin ko dab ganin abun ya fito ta bangaren Mai Martaba dole su kwatanta adalci domin ya nuna musu hakkin yarsa yake son a bi masa, abu na biyu kuma ba za su so wani likitan mai zaman kansa ya bata musu suna ba. A gidan Momy na wuni ni da Mama domin bayan Hamma ya aje ni sai ya shiga gari, muka wuni muna ta maganar likitan har ake dauko zancen wasu likitocin masu taimakon da gaske da kuma wasu masu halin Asim sai dai su ba su kai shi ba ba domin na shi ya yi yawa ba kowane mai imani ne zai aikata haka ba. Daga bisani Mama ta dauko min labarin yayan Ammy da wasu yayan yayyunta ke so, wai magana har ta yi nisa ta kai gurin Mai Martaba ana zancen yin baiko. Na jidadin sosai jin cewar yaran Ammy ne duk dai Mama bata rike sunansu ba, amman ina ayyana cewar Humaira ce da Anty Zee, sosai na so ganin fuskar Mama Fulani da Maryam dan na san ba zata jidadi ba, saboda ba son shiri da Ammy take ba, kuma babu wanda zai so y'ar kishiyarsa ta samu jiki ta sa bata samu ba, balle Mama Fulani dake ta falako a cikin gida da nuna isa. Lallai Allah mai yadda ya so, kuma sai ya bawa Ammy surukai a cikin jikokin Mai Martaba yayan masu arziki wanda nasan Mama Fulani ce zata fi kaunar hakan. Sai da dare muka koma gida, bayan Mai Martaba ya sake Kiran mama ya fada mata cewar an saka wani ranar Assabar mai zuwa wato nan da kwana biyu kenan. Kamar yadda ya saba yau ma sai da siya mana dan abun tabawa a baki sannan ya muka isa gida yana rike da hannuna kamar ba zai sake ki ba. *** *** *** Gaba daya al'amarin duniya ya koma mata sabo kuma ya zo mata ta inda bata zata ba, bayan daukakar da Allah yai ma Ataa akansu ya daukakata fiye da su sai kuma Allah ya kawo ma yaya Ammy miji daga cikin zuri'ar da tai kwadayin yayanta su samu, har magana ta fara karfi ga nata yayan babu wanda ya taya ban da Kamal shi ma Kamal din ma tun da akai fada da shi akan Ataa be sake kula Maryam ba. Balle Rukaiya ita ko zancen ba a ayi yadda kasan ta kasa kashi haka take, ga shi ba kyau ne babu ba amman babu mai gani ya taya kamar wanin abun amai. A yadda take so ita bata ki an hade su da auren Muhseen da za ayi ba, ita ta wanke su gaba daya ta huta ya zamana baby ce kawai ta rage mata. Fitowa tai daga kitchen ta nufo inda Maryam take zaune tana lasar waya ta fara mata masifa kamar mai jin haushinta. “Ai dole ku rasa mijin aure, ina can ina aiki kina nan kina lasa waya, idan safiya ta waye dakinku kawai kuka iya gyara kamar ku? Ace ba za ku iya aikin komai ba? Idan ma kun yi auren ai ba duka namiji ne zai dauki haka ba, dan ba ko wane namiji na kamar Aliyu ba da zai yarda da hali irin na Rahma wanda yai kama da halinku, su yayan Ammy haka suke? Indai auna nan ai su suke mata komai ku gyara ko'ina girki ne kawai nata shi ma wata rana su suke yi, gashi nan ai Allah ya basu maza a cikin waenda nai muku burin samu saboda ku ba ku san ku yi tausayina ko idan ina abu ku rika min ba, duki ki ga yarinyar Ataa haka ta zo tana aiki a gidan tai nan ta yi a can gurin Ammy duk akan mahaifiyarta kuma da Allah ya tashi bata gashi nan har Muhseen da Aliyu sai da sukai fada akanta, kuma yanzu gashi nan Aliyu take aure, mai taimakon uwa ai baya faduwa amman ku kullum kuna kan waya sa kan gado sai ka rantse kujera sai idan na gama ku taso zuwa dinning room dan ba ku da kunya” Maryam ta kalleta cikin jin haushin fadan na ta ta ce. “Oh Mama yau kuma duk wannan fadan a kan mu? Kamar dai kin gaji da ganinmu” “To wace uwa ce zata so yayanta kamar ku su zauna a gida suna jera tsawo da ita? Yanzu idan an wanke Zainab da Humaira ai kubkadai kuka rage domin na ji Abbah ku na zancen har da Batula zai aurar tunda tana da mijinta amman ku ko mai sallama babu, balle mai zancen aure ko a wayar nan da ake haduwa da maza ku ban ku, ace kuma tausayina da yanzu kuma Allah ya tauyasa muku ya baku inda za ku huta ku jidadi” “Mama kin san aikin nan fa ba mu saba ba, taya jiki irin nawa zai iya aikin wahala dan girman Allah? Kara dai a nema wata nai aikin” “Wallahi ba zan dauko wata mai aikin ba, wato n dauko wacce Aliyu ya aure yanzu kuma na dauko wacce ubanki zai aure ko? To ba za a koma ba” Mama Fulani na rufe bakinta Rukaiya na shigo cikin falon makkale da waya a kunnenta baki har kunne tana wasa da keys din motar hannunta, zaunawa tai kusa da Mama Fulani a lokacin da ta sauke wayar ta rumgume Mama Fulani tana murna kamar wacce akai ma albishir. “Mama ke dai wani ne na hadu da shi, ya hadu Mama ga motarsa yar yayi” “A'ina?” Mama Fulani ta tambaya baki a sake Maryam kuma ta tashi zaune tana jin kamar ita ce. “A gidan mai shi ya biya min kudin mai aka cika min motata tam, sannan ya karbi number wayata yanzu haka ina isowa yana kira wai na ji na isa lafiya, yana ta tambayar gidanmu” “Wow Allah yasa mijin ne yanzu nan Mama take ta fada sai ka ce mu muka dorawa kan mu bakin jini” Cewar Mama. Rukaiya ta kyalkyale da dariya tana kara rumgume Mama Fulani da ke murmushi cikin jindadi. AG cera ya zo domin ya temaki garkuwan jiki da kuma lafiyar jiki. Sinadari ne wanda ze magance matsaloli da dama wadanda suke hana garkuwan jiki aiki yadda ya kamata ko kuma yake rusa garkuwan jikin ita kanta. Cututtukan zamani daban daban sun sa mutane gaba kuma magance su yana da wahala; irin ciwon Sugar, hawan jini, ciwon sanyin kashi, ciwon gabobi da sauran su. Haka ma cutukka irin wadanda suka shafi fatar jikin wadanda sun hada da kyasfi, pimples, takurewar fata, rakainuwar fata da kuma haske da kyallin fata duka ana shan AG cera kuma yana temakawa wajen magance illolin nan. Mutane masu fama da rashin karfin jiki wajen kwanciya da iyali da kuma mata masu fama da yawan ciwon mara lokacin al'ada ta karshen wata suma baa bar su a baya ba. A takaice dai AG Cera yana temakawa wajen magance cuttukka daban daban wadan ke damun mutum. Domin karin bayani ku tuntuni mu a wannan number +60167474649 ko kuma ku ziyarci shafin mu http://agnutritioninternational.com.Kamar yadda aka aje cewar Assabar za a koma, haka kuwa akai duk kuwa da kasancewar ranar ba a aiki amman a haka muka tafi ashe su suna shiga office saboda irin wannan case din har sun fi son ya fada weekend saboda kowa ya samu halarta. Kamar yadda akai wacan karon wannan karon ma haka kai daga gurin zama har mutanen su dai.   Sai dai mun samu karin Shukura wato nurse din da fada cewar ita ce shaiduna. Ko da wasa Doc Asim be kalli inda take ba, sai dai ni da Mama yana ta kallonmu kamar be taba ganinmu ba, ya rame sosai ba kamar wacan lokacin ba idonsa har sun fito saboda ramar da yai. ‘Ai baka ga komai ba tukuna’ Na fada a raina ina kallonsa cikin jin haushinsa da kuma jindadin abunda zai same shi. A bangare daya kuma ina dan jin tsoron kar Shukura ta ki fadar gaskiya wata kila ma ya siye ta ballantana a asibitinsa take aiki. Sai da suka gabatar da wasu abubuwan sannan suka fara da tambayar ko Shukura ta san ni, haka ta tsura min ido tana ta kallona kamar bata gane ni ba, na san na yi kiba na kara kyau jiki da sura saboda samun jindadi da kwanciyar hankali da nake samu a yanzu, amman ba zai iya zama wani canjin siffa da zai saka Shukura ta kasa gane ni ba. “Eh na santa” “Kin san sunanta” “Ba zan iya tuna sunanta ba, amman kamar Ita ne ko Aita na manta dai” “A ina kika santa?” “Asibitin da tai jinyar mahaifiyarta” Sai da suka tambaye ta a wace Asibiti ne kuma ko ta san wanda ya kula da mu da kuma ciwon da yake damun mahaifiyata. “Asibitin Doc Asim, na yi kula da ita a lokacin idan ina duty kuma Doc Asim shine likitan da ya duba ta” Sannan suka bukaci na ta fada musu gaskiya tsakani da Allah abunda ta san yana damun mahaifiyata. “Ciwon koda ne” “Me kika sani a gake da Doc Asim?” “Litane kwarare mai asibitin kansa wanda na ke aiki a ciki” “Mun kira ki a nan ne saboda ki bada shaidar akan zargin Doc Asim da ke na cire kodar mahaifiyar Ataa ba tare da saninta ba, har ma tana ikirari ke kika bata shawarar ta dauke mahaifiyarta daga Asibitin ta kai ta wata idan ba haka ba zata iya rasa ta, kuma kina ta yi mata alama da kada ta saka hannu a takardun” Kallona tai ta hade gayu kamin ta kalli Doc Asim sai kuma ta kalli masu yi mata tambayar ta gyada kai. “Na bata shawarar ta dauke mahaifiyarta ta kai wata asibitin saboda samun lafiyarta, kuma tabbas Doc Asim ya cire mata koda domin tare da ni akai tiyatar kuma a gaban idona Ataa ta saka hannu a takardun, sai dai ba zan iya bada shaidar cewar ba da saninta aka cire kodar mahaifiyarta saboda ba a gana aka yi wannan maganar ba” “Amman miyasa kika girgiza mata kai?” “Ina girgiza mata kai ne, saboda karta saka hannu a takardun da bata masaniyar komai a kansu” “Ba mu fahimta ba ki mana bayani dalla dalla yadda za mu ga ne” “Takardun da Ataa ta saka hannu ba ita ce ta farko da take saka hannu a akan irin waennan takardun ba, ita ce ta uku daya an yi gabana na ta ma anyi a gabana dayan kuma labari aka ba ni” “Mi takardun suka kumsa” “Siyar da wani bangare na jikin dan'adam” “Kina nufin Ataa ta siyarda kodar mahaifiyarta kenan?” “Ba ni da tabbacin wannan, idan ma ta siyar ko akasin hakan ba a gabana akai komai ba, sai daia gabana Doc Asim ya rika hannunta ya saka hannu a takardar saboda bata iya sakawa kasancewar bata san komai a boko ba” “Taya akai kika san cewar bata san komai a boko ba?” “Ita ta fada min kuma a lokacin daya bata takardar ya ce ta saka hannu sai ta fada masa bata iya komai ba bata san inda zata saka hannu ba, wannan shine kawai abunda na sani” “Miyasa kika ce ta dauke mahaifiyarta daga asibitin?” “Saboda waenda suke jin irin nata daga karshe suna rasa ran waenda aka cirewa koda cikin asibitin” “Su wa da su waye?” “Akwai wata Hadiza Salisu wacce take unguwar mabera, da kuma Faruk Abubakar da ke unguwar Minannata sai kuma wannan Ataa din da ke unguwar Clapperto road” “Za mu je da ke mu taho da su sati mai zuwa, au bada shaida a gabanki kin yarda” “Na yarda” Daga haka aka bawa Doc Asim damar magana sai ya sake nanata cewar shi saiyar masa da kodar Mama nai. Sai dai sun tuhumi she da siyen koda ba tare da neman yan'uwan masu ita ba, taya zai siye koda a gurin yarinya kamar ni bayan mahaifiyata bata cikin hayyacinta ba tare ya nemi yan'uwanta ba, kuma ya kamata ace akwai shaidu a tsakani. Ni kaina sai a lokacin na kawo wannan tunanin a raina, lallai ya kamata ace ko a iya yan'uwan suka kai ya nemo su indai har da gaske ne, tun daga nan kowa ya san akwai cutar da yake shirin yi. Mun dawo gida tare da Mama kamar yadda muka saba a gidan Momy muka wuni sannan muka wuce gida. A ranar Hamma yai min ba zata da wani form na makarantar koyon girki da ke nan cikin sokoto, ni ban taba sanin cewar akwai wata makaranta ta koyon girki ba na sai yau ashe abun na manya ne wai har certificate suke badawa ga wanenda aka koya musu suka iya. Babban abun jindadi daya fada min cewar sati mai zuwa zan fara zuwa domin yayi magana da malamar har ya kai mata hotona da sunana da duk wani abun daya shafe ni. Na jidadin sosai da yai wannan tunanin ni kaina na san akwai abubuwa da yawa da ban sani ba kuma ban iya ba ta fannin girki abunka da wacce bata saba ba hasali ma ba ya na ke ba a can baya sai idan an samu ganima, wacan lokacin taliya ce muke ci sai kanzo da shimkafa idan ta yi afki. Sai dai an san shiga wannan makaratantar koyon girkin zai taimaka min sosai. Bayan sati daya da wacan taron muka sake komawa sai da wannan karon bayan Shukura har da mutanen data fada cewar su ma an cire musu wani bangare na jikinsu, sun bada shaida kamar yadda Shukura ta fada, kuma dukansu kodar aka cire musu da alama dai Doc Asim ya kware a bangare cire koda ko samar da kodar a gurin masu nema a biya shi ta hanyar kwarai ko akasin hakan. Da aka tambaye su shin suma ba su da ilmi na kamar ne dayar wacce ta kasance matar aure ce kuma babbar mace ta amsa da eh. Ta saka hannu ne saboda bata san komai a kai ba, kuma ta fada mata yayarta na da ulcer dole ai an mata tiyata ashe dan ya cire kodar ne. Namijin ma be saka hannu a takardun ba an likitan ne ya saka hannu da kansa sai ya bashi dayar ya saka hannu wacce ita ce akai wa mahaifinsa aiki akai da sunan kodarsa daya ta lalace zai masa aiki a kyauta. Ba karamin mamaki sukai da jin lamarin ba, da aka nemi jin ta bakin Doc Asim sai ya amsa da cewar shi dayar ce kawai ta siyar masa da koda sai kuma ni amman sauran duka akan ciwonsu yai musu aiki. A lokacin da aka tambayeta ya akai ta san koda aka cirewa Yayarta sai ta amsa da cewar ita ma dai ta yi gwaji a wata asibitin kamar ni su suka fada mata cewar an cire mata kodar, sai dai ganin cewar ba su da inda za su sake kaita a karbetaa bata magani mai tsada da zata ji sauki yasa suka dawo da ita asibitinsa har ta rasu a nan, dukansu su ukun nan sun rasa majinyantansu shi namijin ma sai a yanzu yake gane cewar an cire wa mahaifinsa koda, sai dai biyun kamar ni ne wato talakawa masara galihu waenda ko za su ihu su nuna fushinsu da bakincikin da bacin rai ko son daukar mataki babu mai kawo musu dauki ko kula balle har ya shige musu gaba gurin karbar hakkin na su, ni ma din ba dan da Mai Martaba ya shiga ciki ya mika lamarin a gurinsu ba da ni da su duka ba za a karbo mana hakkin mu ba, babu wanda zai san da zancen an yi mana haka din idan kuma har mu kai unkurin yin wani abu na hukunta shi zai siye masu kamar yadda yai min, amman idan daga manyansa ne matukarvsuna son adalci dole su bi gaskiya kuma su kwato mana hakkinmu su kuma wanke kansu daga bata musu da aiki da yake kokarin yi. Ba mu bar gurin ba sai da suka suka fada mana cewar za su tisa keyar Doc Asim kotu tare da na su hujojin idan sun kara bincike, hakan kuma ba ni kadai yai ma dadi ba har da sauran mutanen. Balle kuma Nana da ba a magana, sai dai sun bukaci dukan mutanen da ni kaina mun kawo takardun da suka nuna hakan kuma suka ba ce za su kai Mama asibiti su sake bincikawa. Gobe zan yi long post In-Sha-Allah 🙏uzuri ne ya rike ni yanzu nai typing wannan. AG cera ya zo domin ya temaki garkuwan jiki da kuma lafiyar jiki. Sinadari ne wanda ze magance matsaloli da dama wadanda suke hana garkuwan jiki aiki yadda ya kamata ko kuma yake rusa garkuwan jikin ita kanta. Cututtukan zamani daban daban sun sa mutane gaba kuma magance su yana da wahala; irin ciwon Sugar, hawan jini, ciwon sanyin kashi, ciwon gabobi da sauran su. Haka ma cutukka irin wadanda suka shafi fatar jikin wadanda sun hada da kyasfi, pimples, takurewar fata, rakainuwar fata da kuma haske da kyallin fata duka ana shan AG cera kuma yana temakawa wajen magance illolin nan. Mutane masu fama da rashin karfin jiki wajen kwanciya da iyali da kuma mata masu fama da yawan ciwon mara lokacin al'ada ta karshen wata suma baa bar su a baya ba. A takaice dai AG Cera yana temakawa wajen magance cuttukka daban daban wadan ke damun mutum. Domin karin bayani ku tuntuni mu a wannan number +60167474649 ko kuma ku ziyarci shafin mu http://agnutritioninternational.com. Na fara zuwa makarantar koyon girki da ke badon 3bedroom, a ranar da aka fara da sabin dabibai. Ban wani sake sosai a ranar ba saboda ina jin kunya da nauyi saboda yawan daliban da ke gurin, malamar ta rubuta mana abubuwan da za mu siyo da kuma abubuwan da za mu fara koya.   Kamar wasa na fara maida hankali ina koyon dukan abubuwan da suke koya mana, wani lokacin idan na dawo gida kuma sai na gwada, da na fara sabon da yan mata da kuma wasu sabin aure da suke makarantar sai ya zama idan ma naje bana son dawowa saboda samun kawaye da nai kuma kawaye masu mutuncin da sanin ya kamata. Mun yi musanyar number wya da wasu daga cikin yan matan da kuma matan auren, yawan matan auren da suka girmi sai dai na kira su da Anty ko Maman wane saboda ina jin nauyin fadin sunansu hakan nan kawai wasu su kira na da yata kasancewar ina da sunan yarsu wasu kuma su ce min kanwata. Daga lokacin na fara fa'idantuwa da wayar da Hamma ya siyo min, domin ta nan nake chat dasu idan sun ga wani abun mai amfani sai min sharing su tambayi tafiya da ta miji, masu grps suka saka ni wata babban a cikin mu kuma ta bude mana wani grp na koyon girkin d muke, wai ko da akwai abunda Malama tai jawabi wanda mutum be gane ba sai yai tambaya a fada masa ko a kara wayar masa da kai. Na kara ilmi ba kadan ba, domin a cikin groups din da nake ana yawan turo abubuwna da suka shafi matana aure na inganta zamansu yadda za a iya kula da miji yan'uwan miji da sauransu, a cikinsu akwai wani wai shi Women Diaries na wata marubuciya, ina karuwa da grp din sosai abunda ban fahimta ba kuma sai nai tambaya a take za a fayyace min komai.    Daga ranar da akai wacab case din ba ba su sae kira ba, har na sawon wata daya, sai da suka kara bincikensu suka tattara dukan hujojinsu suka tabbatar da abunda ake zargin Doc Asim da shi bayan sun tsananta bincike sannan suka mika shi kotu. Wani abun mamaki Doc Asim har da daukar lauya mai kare shi, ni da Mama ma lauya ne yake tsaya mana duk wani abincike ko gabatar da shaida shi yake yi. Hakan ya saka wani lokacin ba da ni ake zuwa kotun ba domin cikin nawa wani lokacin sai ya taso min da zazzabi wani lokacin kuma kamar ba ni ba. A cikin wannan halin Hamma ya dauke ni muka koma Abuja daman wani lokacin  yana tafiya yana dawowa saboda aikinsa, ni kuma baya son tafiya da ni saboda koyon girkin da nake. Yanzu kuma na kamalla daman ajin akwai na wata daya akwai na wata biyu uku hudu biyar har shakera uku ma ya danganta da wanda ka zaba. Ni kuma ya biya min na wata biyu ne kawai kuma babu laifi na iya abubuwa da dama na zamani da kuma irin na da da ake saffarawa a girka tun daga kan na sha wato home drink's har abincin. Wani abun kuma ina ra'ayi zan leka YouTube na duba na fada masa ya siya min kaza da kaza idan babu ina son na hada. Muna saura kwana biyu muje Abuja Hamma yake fada min zancen baikon da za ayi ma Amina, na yi murna sosai ina jin na taka wani da za a kira matar yaya kuma a fada min wani abun na kanen mijina idan za ayi. Sosai na so mu fasa zuwan har sai an yi baiko amman Momy ta hana saboda tana son na walkilce a gidan Mama Fulani na kai lefen Muhseen da za'ayi wanda ba zata samu zuwa ba saboda baikon Amina ita ma Mama Fulani ba zata samu zuwa ba saboda kai lefen.   A ranar da muka sauka Abuja a gidan Mama Fulani muka sauka kamar yadda Hamma ya saba idan yayi tafiya zai sauka a gidan Mama Fulani idan a sokoto ne kuma zai sauka a gurin Momy. na yi mamakin yadda muka samu Mama Fulani ta murje ido kamar ba ita ba, sai marhabun take mana da far'a da komai irin yadda take tarbar Hamma, tana ta nuna kulawarta akaina ni dai ban sake jikina sosai ba sai dai na lura hakan ba karamin dadi yai ma Hamma ba, ba ita kadai ba har su Maryam da Rukaiya sun murje ido suna sakewa da ni kamar komai be faru ba, ni kuma na kasa mantawa a duk lokacin da na kalle su ko kuma suka min wani abun na karramawa ko kulawa sai na tuna da baya. Suna ta shirye shiryen kai lefen Muhseen da za'ayi kamar yadda Momy ta fada. Sai da muka huta a gidan sannan muka doshi gidanmu da ke can Abujar, an gyara ko'ina na gidan kamar muna ciki muna rayuwa. “Na yi mamakin ganin gidan nan a haka, haka wacan zuwan na tararda gidan wanke fes” “Gyarawa ake” “Wa ke gyarawa?” “Aljanu” Ya fada yana kanne min ido kamin ya fada min cewar mai masa gyaran fulawoyi da gida ne yake gyarawa. Washe garin ranar da muka so ya kama Saturday a ranar a aka kai lefen a wata unguwar masu hannu da shuni da ke garin abuja, lefe na mai amsa sunan lefe da babban gida na masu naira irin dai wanda Mama Fulani take kwadayi kuma take so. Sun yi mana goma ta arziki bayan kayan ciye ciye har da kudi masu yawa suka hadu mana. Ni dai ina so ganin yarinyar domin Hamma ya fada min wai ya ganta a wayar Mama Fulani tana da kyau sosai.   Bayan mun dawo mun huta ina bangaren Ammy na shiga whatsapp dina sai ga hotonta da aka hada da na Muhseen da kuma lefen ana tayata murna a status din Husna na gani, gaskiya kyakkyawa ce sosai fara mai jiki sai dai ba sosai ba, ban yi mamakin kyauta ba daman can irinta yake ai, wato mace mai kyau na san da hakan tun daga lokacin da aka kawo ni aiki a gidansu, kyau na cikin abunda yake burge Muhseen, kuma ba laifi ba ne dan ya so mace mai kyau musulunci ma ya yarda a auri mace dan kyauta.    Daga gidan su Mama Fulani aka aiko mana da na mu kayan baikon Amina, ta bangaren Abbah da yake akai komai da shi, a lokacin da aka kawo mana na mu na sha dariyar Hamma saboda korafin da ya rika yi wai nawa ya fi na shi yawa, kuma haka din ne nawa dabam mai yawa na sa kuma ba mai yawa sosai ba, a waya Momy take fada min wai mai yawan shi ne nawa wata kila ina da kawaye da zan rabawa na jidadin da Momy ta kwarrama ni ta tabbas da ace ina da kawaye a nan Abuja babu abunda zai hana ni raba musu baikon kanwar mijina. Sai dai kasancewar kawayen da nai sabo da su yan makarantar koyon girki ne kuma duk a sokoto suke babu daya a nan. Sati daya da kai lafen Muhseen aka kawo baikon Rukaiya na ni kadai ba, har Hamma sai da yai mamakin jin zancen ta samu miji domin shi kansa be san wani na nemanta ba, daga ni har shi har su Momy mun ji abun ne daga sama, a ranar da Abbah ya fada masa za a kawo baikon sai da ya kira Mama Fulani a waya yana tambayar anya dai an yi bincike akan mutumen kuma an san waye shi? Ina jin lokacin da Mama Fulani take fadar wai ai yanzu an daina zufafa wannan binciken da ake kuma yaron dan kano ne iyayensa sun zo har da wamban kano (Fake Name) ya fada musu shine babansa kuma sunansa yake bearing, dan haka ba sai an fadada bincike fa, aiki kuma shine manager a gidan man da ke nan Abuja. Tana ta fada masa irin kudin da ya kashewa Rukaiya daga haduwarsu zuwa yau ya kashe mata kudi masu yawa, gashi kuma Abbah yana zancen hade yayan Ammy su uku da Muhseen ai kara a hada da Rukaiya tun da ita din ta samu kuma yace a shirye yake. Ni kaina na yarda da zancen Mama Fulani cewar mai kudi ne tun daga kan kayan baikon da ya aiko kayana masu yawan da gaske irin waenda ake kaiwa a manyan gidajen, a ranar Momy ta zo har da Daddyn ma da wasu yan'uwan Mama Fulani da ke Yola. Kamar yadda Hamma yai min alkawarin saka ni a wata makarantar be saba alkawarinsa ba, duk kuwa da kasancewar cikin nawa wata biyar ne ya lokacin har da yan kwanaki a kai, amman a haka ya aminta ya saka ni a Royal Academy, wata makarantar kudi ce da ke nan Abuja ta masu koyon karatu da rubutu da kuma waenda ba su samu damar kare karatunsu ba kamar ssce.   Karfe tara ake zuwa a taso sha biyu ga irin mu ga yan sss2 da 3 kuma suna zuwa da safe misalin takwas su tashi biyu saura. Gaba daya makarantar da turancin ake magana tambaya da kuma bada amsa ko da kuwa tsakanin dalibi da dalibi ne, ma ji tsoro sosai ganin irin ka'idar makarantar sai dai hakan ya saka na kara dagewa da maida hankalin wajen ganin nima na iya turancin kamar sauran, ba musulmai kadai ba ne a makarantar akwai kistoci ma har da waenda ba hausawa ba, akwai matan aure da yan mata a ciki akwai maza akwai mata sai dai bangaren mazan dabam matan ma bangarensu dabam, ko a cikin matan daga ni sai wata haulatu ne muke saka niqab domin ita ma ina jin mijinta irin Hamma ne mai tsananin kishi, ba niqab kadai ba har safar kafa da hannu Hamma cilasta min sakawa yai yi. A dole kuma mai hakan saboda ina son karatun. Shi yake kai ni ya dauko ni idan mun tashi, idan ma ba shi da time sai dai ya ce na jira shi idan ya gama ya zo ya dauke ni, wani lokacin da yar  kula ta abinci kamar wata karamar yarinyar yar makaranta ko da yake ba ni kadai na ke zuwa da abincin ba, kuma duk wanda ya gan ni da abincin idan ya lura da yadda cikina ya fara dan tasowa zai san ai lalura ce, domin kuwa cikin nawa na kara girma cin abincin na karuwa abun har mamaki yake ba ni. Sosai na ke son zuwa Nijar gurin Yan'uwan Mama da na Babana na ga waenda ban gani da Waenda kuma na gani na kara ganinsu, duk kuwa da kasancewar sun zo a baikon da akai ma Zainab da Batula na cousins, sai kuma na Humaira da akai kwana biyu da yin na su, aka saka lokacin auren daya da na Muhseen kamar yadda Abbah ya fada cewar yana son ya hade su yai musu auren a tare a bar Maryam kawai ita da bata samu mijin ba. Karatun da na ke a yanzu ya fara zame min kamar da wahala saboda na hada biyu ne, da yamma ina zuwa wata makarantar islamiya ta matan aure wacce ake zuwa karfe uku a taso budu da rabi, a can ma na yi kawaye amman iyakana da su a makarantar wai kuma a waya da muke chatting. Ga kuma cikina da shiga wata bakwai da shi a yanzu, ba wata wahalar na ke ba bayan nauyin da cikin ke min sai kuma yawan zazzabin da tsandar abinci, sai dai bana nunawa a gaban Gogan nawa saboda na san halinsa yana ganin wani abun zai iya hana ni karatun ko yanzu da be ga wani abun ba yana fadar wahalar tana ma cikin yawa balle kuma ya gono ai a take zai hanani zuwa makarantar.   Wani iko na Allah sai na fi gane makaratun arabiya fiye da na bokon da na riga farawa kuma na dan gane wasu aabubuwan a baya domin na iya karanta hausa tun kam na shiga makarantar, bokon ma ba zan ce bana ganewa ba amman na fi gane na arbiyan fiye da na bokon.      Wata biyu da kai lefen Muhseen akai soma shirye shiryen biki, tun kan 25 Sept aka soma baki a gidan Mama Fulani ciki kuwa har da su Momy da wasu daga familynta da suka zo bikin, da mutanen yola. Abbah ya gyara ko'ina na gidan an yi sabon fenta an sayo abubuwan tarbon baki da na hidimarsu. A Abuja aka fara komai na bangaren Mama Fulani ta bangaren Amaryar Muhseen kuma daga Bachi aka fara sannan aka dawo Abuja aka cigaba da shagali. A cikin shagalin biki wani wani labari marar dadin ji ya zo mana, Waenda aka tura su je yin jere Rukaiya sun tararda da karamin gida mai ciki da falo daya da bandaki sai kitchen a tsakar gidan, ma'ana dai irin gidan nan na talakawa masu rufin asiri, yadda Mama Fulani ta sha kuka a ranar abun har tausayi ya bani ba ita ba ba Rukaiya ba ba yan'uwanta ba, Momy ma bata jidadin hakan ba sai dai babu yadda aka iya. Ai ko a lokacin ne Hamma ya hau fada cewar daman can sai da ya ce ayi bincike Mama Fulani tace bincike ba dole ba ne kuma an san iyayensa da sauransu. A lokacin ne Abbah ya kiran Mahaifin yaron yana fada masa awai an je jeren dakin an tararda abunda ba a zata ba, sai Wamban kano yake fada masa cewar ai ba shi ya haife shi ba almajirin gidansa ne tun yana matashi har ya tasa ya koma Abuja yana neman kudi, a gidan man ma shi ba manager ba ne yana cikin amsu siyar da man ne dai a tanki. A ranar Rukaiya suma ne kawai ba tai ba akan bakinciki ita da Mama Fulani. Hamma ne ya saka aka nema masa wani gidan haya mai kyau aka je can akai jeren. Washe garin ranar da akai Walima akai Dinner, sai da kowa ya halarta sannan daga baya ni naje tare da Hamma, na sha kyau abuna ni kaina na san na yi kyau domin lace din angon blue ne mai fitar da farin mutum, ga kuma tsoraye na aka min suka sauko har bayana, kuma nai sa'a Hamma ya bar ni na fidda abuna sai dai be barni na yafa karamin gyale kamar yadda kowa ke yafawa ba nawa babba ne amman hakan be hana ni yin kyau ba, da man kyau mace ba a fitar da surar jiki ba ne daga kyau tufafi ne da ainahin halittar da Allah yai ma bawansa. An zubar da kudi sosai a gurin karin har nake ganin kamar hakan be dace ba, angwaye da Amare sun sha kyau sosai, duk inda Hamma yai yana rike da hannuna karin ma bayan yayi musu sai ya dawo gurina yana ta min karin ni ko har kunya na ke ji saboda cikin jikina, ban taba daukar cewar Hamma zai iya rawa kamar haka a gaban mutane ba, ba wani rawa yai can sosai ba amman yana takawa a hankali yana wasa da hannuna. Ina tsaye da shi wata cousin sis dinsa ta zo tai masa kari ta dauki hoto da shi, na ji zafi sosai shi kansa sai da ya lura da hakan har yai murmushi.  An yi dinner lafiya washe ya kama Assabar sai aka rabu wasu suka tafi Bachi dauren auren wasu kuma suka tsaya a nan Abuja a inda akai na su Rukaiya da Humaira da Zainab da Batula. A daren ranar da aka daura auren aka tafi da su Zainab da Batula zuwa Agadez tafiyar da akai ta da ni duk kuwa da kasancewar Hamma be so haka ba, ni kuma na lake sai na tafi kuma Momy ta saka baki a dole ya kyale ni a bisa sharadin kwana biyu zan dawo saboda shiga kotun da za ayi. A cikin garin Kaduna aka kai Humaira Rukaiya kuma a kano gidan da Hamma ya kama musu Muhseen kan a Abuja ya tare da matarsa. A gida mai kyau aka aje su su kansu sun san an musu gata, daman mai hakuri mawadaci hakurin zaman auren da Ammy tai ma jureya da tarbiyantar da yayanta da kuma cirewa rai kwadayi sai gashi Allah ya bawa yayanta inda za su huta kuma su jidadi.   Kwana na biyu a Agadez din bayan kai su Zainab da Batula muka dawo tare da Mama da wasu da suka rakota saboda jin cewar zama na karshe ne za ayi, washe garin ranar da muka dawo ya muka tafi sokoto har Hamma saboda case din. Ranar da muka isa ranar aka shiga kotun wani abun da zai baka mamaki har da yan jarida abun ban san taya suka ji ba ko da yake abun duniya baya boyuwa. Alkalin ya yanke hukunci ne akan kwararan shidu da kuma hujojin da aka gabatar a gaban Alkalin.   Hukuncin shekara ashirin da biyar alkalin ya yanke masa daman tun da aka soma case din aka rufe asibitinsa, sai gashi kuma alkalin ya hada da asibitin cewar a rufe ta gaba daya. Kamar wanda akai aka yi ma albishir da mutuwa haka Doc Asim yai da fuska da ya dafe kansa. Mu kan ran mu fes domin yan yanke masa hukuncin daya dace da shi, sai dai Alkalin ya ba shi damar daukaka kara zuwa kotun Abuja idan yana ra'ayi. Ban yi tsammanin zai yi hakan ba, sai ga shi lauyansa ya fadi cewar za su daukaka kara zuwa Abuja domin ayi musu adalci a can. A ranar ruwa ne kawai ban zuba kasa na sha ba akan dadi da murna, amman na yi farinciki sosai kuma na yi ma Allah hamdalla, wani abun da ya kara min jindadi da sunan Hamma be fito a ciki ba, hakan na nufin ya saba siyarda kodar kuma wai Hamma ne kawai ya siyarwa ba, domin idan har zai fadi sunan Hamma to zai fadi na sauran manyan ma da ya siyarwa.   Cikina na cikin wata na tara aka fara zuwa kotun Abuja na daukaka karar da yai a wannan karon ma ba mu muke zuwa ba wani lauyan ne yake wakiltar mu.   Asibitin da na ke awa likitar ta fada min Edd na, tun daga ranar Hamma be sake ba ri na tafi makaranta ba fita ma baya bari nai kullum ina gida idan yana gurin aiki kuma yana yawan kirana wai ai wani lokacin ba a lokacin da suke fada mutum ke kaiwa ba wani sai yafi wani kuma ba zai kai ba, siyayya kayan sakawa ta babu abunda be siya min ba, na jariri ne kawai be yi ba wai ba zai siya na mata a haifa masa namiji ba ba kuma zai siya kayan maza a haifa masa mace ba dan haka sai idan na haihuwa zai hada komai na jariri sai dai ya siya wasu kadan da maza ko mata duka za a iya saka musu. Nikan fargabar inda zan haihu ya hanani sukuni ina ta jin tsoro ta yadda da ko ya za su fito cikina duk girman cikina a ce ta nan da zai fito a duk lokacin da na tuna sai hankalina ya tashi, ni da ko motsi cikin yai sai na ji tsoro balle kuma ace haihuwa, wannan yasa na matsawa Hamma akan ya mayar da ni gida gurin Momy na haihu a can ko kuma ya kai ni Nijar gurin Mama amman ya ki har cewa yake wai ko haihuwa nai a gurin Mama Fulani zan zauna ni kan hakan be min dadi ba domin zan fi son zama a gurin Mama ko Momy.   yana gurin aiki na kira shi a waya na fada masa bana jindadi ina jin cikin yana min motsi sosai kuma ina jin ana sukana a baya, da sauri ya zo ya dauke ni muka tafi asibitin, sai aka ce mana ba haihuwar ba ce haihuwar dai tana kusa amman ba ita ce, haka muka kwaso muka dawo gida tare da maganunguna da suka rubuto mana. Sai gani washe gari kamar ba ni na yi kwaliyata na chakire kamar ba ni ba, bakina ya sha lipstick ga wani uban turaren dana zuba na sha doguwar rigar shadda ta na yi daurin dankwalina ture ka ga tsiya. Sannan na shiga kitchen na girka mana jalof din shimkafa da vegetables, ban na sauke na dawo dakina na dauki cingan na saka a bakina sannan na fito falo na zauna rike da wayata ina duba whatspp. Ina jin lokacin da Hamma ya faka motarsa ya fito ya murdo kofar falon ya shigo hannunsa da leda. “Sannu da zuwa” “Kai kai kai Babyna wannan kwaliya fa? Acancan ai wannan kwaliyar kamata yai ace tukuici za a baki, kuma ba abun a baki tukuici ba ga ki da tulelen ciki, da na taba ki kadan ki fara kuka kina cewa bani da tausayi” Dariya nai na unkura na mike tsaye na mika masa bakina mukai wa juna kiss kamar yadda muka saba sannan na karbi ledar hannunsa. “Gaskiya kin yi kyau babyna” “Na gode” “Just” Na kanenn masa ido kamar yadda yake min sai ya kyalkyale da dariya ya rikoni ya zagaye hannayensa da cikina. “I love you, sarkin raki” “Aiko ina da kokari” “Za mu gani idan za ki haihu” “Ai ba zaka gani ba, idan zan haihu sai dai na baka labari” “No ba zan yarda ba, ba za ki haihu hannun namiji ba kuma a gabana za ki haihu da ni za a shiga, kin san fa ance akwai likitocin da suke ketawa mace haddi idan za ta haihu kuma ni ba zan yarda wani ya ganki ba, sai dai mace yar'uwarki” Murmushi nai daman na san za a rina yadda yake yawan nuna kishinsa ba zai iya yarda wani mijin ya karbi haihuwa ta ba, ko jiya da muka je asibitin sai da ya saka aka nemo masa mace ta duba ni. Muna cikin cin abinci yake labarta min an saka auren Amina da Husna on 14 Oct. “Eyyy kamin lokacin na haihu sai na yi gayu” “Da goyon?” “Kai zan bar ma shi ai” Yayi murmushi. “To Maryam fa?” “Maryam har yanzu dai bana jin ta samu wani da ta samu da Mama ta fada min” “Kai har ta bani tausayi Wallahi, ba dadi ayi ta ma wasu aure ana wuce ka” “Koda ai da kaddararsa wani jinkiri alheri ne, kuma da ka yi auren a koma ana kuka ai kara kawai kayi hakuri har na kwarai ya zo, domin duk yadda ta matsu tai auren ba tai Rukaiya ba da ta auri wanda ko boko be yi ba, da ma ace yayi karatun sai a sama amsa aiki amman babu bokon abubuwan sai a hankali wani lokacin haka jarrabawa take zuwa ma mutum kuma komai yana bukatar a tsananta bincike, da yanzu an yi bincike mai zurfi ai da duk haka be faru ba, amman sai aka tsaya ana masa kallon dan babban mutum ganin ya zo nema masa aure kuma yana bin sunansa a matsayin ubansa” “Gaskiya kan abun babu dadi amman kaddara ce, ta riga fata haka Allah ya so” “Na mu kawai Addu'a ne, kuma na fadawa Mama na ce tai ta mata addu'a Allah ya bata miji na gari, ita kuma Rukaiya Allah ya mata mafita” “Amin” Na amsa ina kallonsa ya mike tsaye yana murza ido. “Lafiya?” “Zazzabi na ke ji” “To ka sha magani sai ka kwanta” “To Hajiya ta” Na masa murmushi sai ya mayar min sannan ya dauke plate din da muka ci abincin ya nufi kitchen. Kwana biyu da wannan na sake jin irin wacan ciwon sai dai wannan ya ci uban wacan ta ko'ina domin ba kaina ba ba cikina ba ba bayana ba ba marata ba ko'ina ji nake yana murda min, haka na wuni tun safe har dare kkuma Allah ya bani ikon yin girkina cikin karfin hali har na gama, sai da yamma abun ya tsananta min idan zan zauna sai na ji kamar abu zai fito min da baya, hankali be kara tashi ba sai da naje fitsari na ga jini sannan na kira Hamma a waya na fada masa. Daga office ya dawo gida hankali tashe a lokacin har na fara kuka babu hawaye saboda tsananin azaba. “Innalillahi wa'inna ilaihirraji'u, wayyo bayana wayyo cikina Momy Mama, har da Mama Fulani da Ammy” Su na ke ta fadi har aka shiga da ni dakin haihuwa, bana iya komai dai dai amman ina jin lokacin da akai ta rigima da Hamma kamin a samo macen da zata karbi haihuwa ta. Ihu nake iya karfina su ko sai ce min suke na nai nishi. “Nishin ya kare wayuo Allah Allah ka cece ni, wayyo Allah Wallahi Aliyu ne” Na fada cikin rudewa da jin zafin murdawar da cikin ke min. “Addu'a ake Allah ake kira” Likitar ta fada min hakan yasa na fara karanto addu'ain da na sani a cikin har na neman tsari daga azabar kabari da talauci amman jin anke kamar ana karo min abun, da na ga abun be min ba na koma salatin Annabi. A haka na kwashe awa hudu ban haihuwa tun ina nishin da sauran karfina har karfin ya kare. “Dan Allah ku kira min Momy dan Allah ta zo” “Ba Momy ba ko Daddy ba zai zo ba balle Momy sai da kika zo haihuwa kika tuna da Momy, sai kin ji yadda kowa ya ji” Matar ta fada tana dariya. “Wayuo Allah ka min Rahama Allah na tuba” Na fada ina da kuka sosai, sai ga Hamma ya shigo a cikin dakin duk ya hada gumi kamar shi ke nakudar, hannu ya kama ya rike idonsa cike da kwalla yana ta min addu'a. Cikin ikon Allah da iyawarsa na soma jin abu na fito min, wani uban uhu na kwala sai da ji nai an yanka ni da wani abun an janyo abun sai kuka yake, sai suka dora min shi saman ciki suka ware min kafafuwansa. “Kall ki gani me kika haifa?” “Namiji” Na fada a wahalce sannan sukai dariya suka dauke shi. ALIYU POV. Farinciki ya kasa barinsa ya yarda cewar dansa yake gani, jininsa be san lokacin da ya saki Ataa ya nufi inda Nurse din da ke goge jaririn take sannan dayar ta fita ta karbo kayan jariri, kamin a saka masa kaya sai da Aliyu ya karbi dan yai masa kiss sannan ya mika shi aka saka masa kaya. Shi ya fito rike da abunsa ya nufo inda su Mama Fulani take tsaye a take gurin suka fara ihu da murna. Wannan ya karba wannan ya karba, aka hau yi masa hotuna cikin har da uban yaron ya aikawa Momy kuma ya dora status dinsa. A rana duk wani family member na su sai da yai farinciki da samun haihuwa da Aliyu yai. Sai a lokacin ya gane yana tsananin son Ataa da kaunarta, jin nai kamar na lashe ta yake ji ita da abunda ta haifa ba ma shi kadai ba har da Mama Fulani sai a lokacin da san darajar Ataa. Sosai yan'uwan Nana suka so a ba su Ataa su tafi da ita can, amman Mama Fulani da Momy suka tsaya kai da fata akan ayi musu alfama a bar musu ita a nan saboda Aliyu idan aka maida ita a can ba zai samu damar zuwa ko da yaushe ba ga shi kuma ba zai yayu ya koma can da zama gaba daya, ko yake yadda yake rawar kafarta zai iya tarewa a can sai dai ya nuna musu rashin an ido akan matarsa ko kadansa. An zubawa Ataa kayan barka kamar ba gobe ta kowane bangare samun kyauta take da kulawa sai ta zama yar gata. A ranar suna jariri ya ci suna Muhammad Amir, an yi bidiri an kashe kudi iya kudi, an yi abubuwa da dama na rabawa mutane wani abun da zai baka mamaki har da Mommyn Rahma, dole ta zo ko dan nadamar da tai ga kuma alakar Ataa da dukiyarsu. Kwana uku da bikin sunan aka sake yankewa Asim makamancin hukuncin da aka yanke masa a wacan kotun ta sokoto, yanzu kan babu zancen daukaka kara sai fuskantar abunda ya aikata. Hasara biyu da uku ta same shi ga na rufe asibitinsa ga na bacin suna ga kuma na rufe shi gidan yari. **** **** **** ATAA POV. Sai da nai arba'in sannan na tafi Nijar ganin yan'uwana, wata daya nai a can duk kuwa da kasancewar Hamma be so haka ba amman ban bi ya kansa ba domin na lura idan na biye shi ba zan yi zuminci ba, domin shi ya fi son kullum ina kusa da shi ko dan dansa, naga dangi na kusa da na nesa daidai gwargwado, kuma na ga kauna da soyayya ni da Amir ta ko wane bangare, har sai na ji kamar kar na dawo. Ba Abuja na dawo kai tsaye ba, a gidan Momy na fara sauka sati na daya a can ita ta kaini gurin wasu yan'uwanta da ban sani ba da ma waenda na sani na gaishe su sannan na dawo Abuja gurin Mijina. Ina dawowa Hamma ya daukar min wata dattijiwa mai kula da gina, ni kuwa aikina girka abinci kula Amir sai kuma makarantar da na ke zuwa domin bana wasa da karatuna saboda burin da na ke da shi na yin zurfi a ilmi ko da kuwa Hamma ba zai barni nai aiki ba ina da burin yin zurfi a ilmina Amir na da wata uku akai bikin Husna da Amina, mun chashe sosai mun biki mai amsa sunan bikin har manta nai da ina da da sai idan zai sha nono ake kawo shi da ya sha nonon, yan'uwan ubanshi za su dauke shi bachi kawai ke hada ni da shi. Wani abun tausayin har kuma tsawon lokacin Maryam bata samu wani ba Rukaiya kuma na dauke da juna biyu ita da sauran Amare, matar Muhseen ce kawai bata samu komai ba, daman na san za a rina an sace zanen mahaukaciya na san sai ya gama lokacinsa kamin ya haihu. Na maida hankalina sosai akan karatuna, da kula da mijina da kuma dana, karatu be hana shi ko daya ba, haka ma kula da mijina da na be hanani karatun ba, na dage na mika dukam imani da karfina da dama saboda samun cikar burina. Ga goyon baya da na ke samu da kauna ta ko wane bangare, kan kace kwabo na goge a makarantar cikin shekaru uku ni ma ana dama da ni a cikin daliban da za su shiga aji na karshe wato Sss3 a Royal Academy. Daf da yin Candy na samu wani cikin hakan kuma yayi min daidai domin na san iya lamani Hubby ya yi min na daga min kafa daga haihuwa duk kuwa da irin son yayan da yake har na gama makarantar. A week later akai bikin Maryam da wani mai mata biyu a sokoto dan'uwana Momy da ta hada ta da shi kuma suka daidaita. Ba laifi mutumen na da rufin asiri daidai gwargwado sai dai zaman kishi da zata fuskanta da matan sakkwato wanda za su gyara mata zama ta gane kuskurenta. Cikina na da wata uku Hubby ya sama min admission a american university da ke Abuja, a lokacin da ya fada min yadda tsari da daliban makarantar suke sai abun ya tsorata ni sosai ina ta ganin kamar ba zan iya ba, ashe abun saka kaine kuma karatun ya zo min da sauki saboda na yi nisa a qur'anen ina daf da sauka ma, sai hasken karatun ya kara bude min kwakwalwata, da safe kullum sai Hubby ya biya min na qur'anen a na bokon ma inda ban gane ba yana min karin haske, domin ya fada min abunda ban gane ba na rika tamyarsa ko wata mace, amman be yarda na tambayi wani namiji ba da sunan class mate dina. Makarantar ma kamar wacan sai na rufe komai na ke tafiya shiyasa babu wanda ya san fuskata sai matan da muke shiri da su sosai shi ma waenda suke da contact dina muke ziyarar juna ko suke ganin status dina. Lokacin da na fara zuwa na maida hankalina da kuma yawan tuna burina sai abun ya zo min da sauki, sai dai wannan cikin ba kamar wacan ba ne, wannan na sha wahalar sa sosai ga shi kuma ina farko farkon fara karatun ne. A haka nai ta fama har cikin ya girma a lokacin muna daf da fara exam din shiga ug 2, a haka nai jarabawar cikin wahala Hubby na ta tausayina kamar yadda na saba sai dai baya karya min guiwa saboda ya san burina kenan. Bayan exam da sati biyu na haifi yan biyu duka mata kyakkyawa, wannan karon ma sai da aka min kari kamar dai wacan, a gidana akai bikin dattijiwar da ke kula da gidan ita ke hada ruwan zafi tai ma twins wanka wato mai sunan Mama Fulani da mai sunan Mama na sai akai musu lakani da Nimra da Namra. Bayan wata biyar fa haihuwar twins muka je Nijar bikin Mama da wani dan'uwanta, ni abun har dariya ya ba ni wai Mama za tai aure sai dai na san auren shi ne darajarta da martaba da kuma mutuncinta. BAYAN WADANSU SHEKARU. Wa zai gan ni a yanzu ya ce ni ce a wacan lokacin nai bara da roko a titi, ni ce na sha wahalar rayuwa na fuskanci kalubale na rayuwa kala kala, mai hakuri madawaci kuma wanda ya rike Allah baya faduwa kasa, duk kuma wanda Allah yai masa gata to ya huta kuma ya dace. Na rike Allah na yi hakuri kuma na ci ribar hakurina Allah kuma be barni na yi kunya ba, da duk wanda yake kallona a matsayin banza marar amfani ya koma yana min kallon kamar babu wanda ya kai ni gata ya fini dacewa da komai a rayuwata. Duk wanda ya gan ni a yanzu zai zata daga sama na samu arzikin ko kuma arzikin ya zo min sai wanda ya san wahalan da na sha kamin na samu wannan. Wai ni ce rike da takardar bautar kasa na yi, na yi karatu kan burina na cika na yi degree in business administration amman bana karatu ba ko da yake ina da burin aikin sai dai na san Hubby ba zai bar ni ba. Na canja daga burina na karatun likita zuwa na gadon gidan mu wanda Mai Martaba yake son kowa yai saboda yin aiki a karkashinsa da kuma sanin ilmi akan kasuwanci da yadda zaka iya tafiyar da shi yadda ya dace. Al-hamdulillah ko a haka rayuwata ta kare ba tare da na yi aikin da Hubby baya son nai na samu abunda na ke kuma na gode Allah na, wata kila a gaba ya canja ra'ayinsa ya bar ni na cigaba da karatun wata kila kuma ba zai yarda ba, daman kuma ba duka buri ne yake cika ba, ba komai ake nema a samu ba, ba kuma duk a abunda kake so ne alheri a gurinka ba, sai dai ba zan kasa gode masa ba akan dukan kulawa da goyon bayan da ya bani har na samu cikar burina da ba ni damar amsa sunana AISHA UMAR MRS ALIYU MUHAMMAD. *AL-HAMDULILLAH* Dukan yabo da godiya su tabbata ga Allah mai kowa mai komai wanda ya ba ni ikon rubuta littafin mai suna Z A K I da kuma kareshi cikin koshin lafiya da kwanciyar hankali. Na sadaukar da wannan littafin a gareki Mama Aisha Kabir A A Ladan. Godiya ga dukan masoyana waenda suke cikin paid groups, na gode sosai da irin kaunarku a gareni Allah bar kauna. Waenda suka karanta ba su biya ba kuma na bi ku bashi indai hakkina ne. Sai mun hade da ku a littafi na gaba idan mai rai da lafiya ya yarda. Ba littafi ne irin na yau da kullum ba littafi ne da zai tabo wani bangare na rayuwar wasu mutane da kuma wata macen da kaddara ta fada mata. Ba kaddarar talauci ba ce kamar ta Ataa (Zaki) Ba kaddarar Aure ba ce kamar ta Nawwara (Rai Biyu) Ba kaddarar soyayya ba ce kamar ta Zinneera (Zabin Rai) Ba kaddarar gudun iyaye ba ne kamar na Namra (Zagon Kasa) Ba kaddarar asiri ba ne kamar na Hafsatu Manga (Hafsatu Manga yarinyar kauye) Ba kaddarar rashin uba na gari ba ne kamar na Jodo (Khadijatu) Ba kaddarar Ciwo ba ne kamar an Minal (Babban Goro) Ba kaddarar kauyanci ba ne kamar na Maryam (MAIRO) Kaddara ce dai wata ta dabam, wata kalar kaddara ce bata rashin gata ko ilmi ba ba kuma ta shashanci ko wauta ba. Labari ne tafe da rayuwar wasu mayu, da suke cikin wata alkarya. Labari ne mai maida mace namiji ba, namiji a siffa da kamani, namiji a zuciya da jini. Labarina na wata duniya biyu mai cike da abun mamaki da al'aji, labari mai hada Kasar Katsina da Bauchi a wata hadaka ta ba zata. FULANI labari na daman na Fulanin asali❤ *Daga yar Mutanen turankawa Fulanin kwarai, jinin Shehu Khadeeja Candy ce👌Yar mutane sakkwatawa* AG cera ya zo domin ya temaki garkuwan jiki da kuma lafiyar jiki. Sinadari ne wanda ze magance matsaloli da dama wadanda suke hana garkuwan jiki aiki yadda ya kamata ko kuma yake rusa garkuwan jikin ita kanta. Cututtukan zamani daban daban sun sa mutane gaba kuma magance su yana da wahala; irin ciwon Sugar, hawan jini, ciwon sanyin kashi, ciwon gabobi da sauran su. Haka ma cutukka irin wadanda suka shafi fatar jikin wadanda sun hada da kyasfi, pimples, takurewar fata, rakainuwar fata da kuma haske da kyallin fata duka ana shan AG cera kuma yana temakawa wajen magance illolin nan. Mutane masu fama da rashin karfin jiki wajen kwanciya da iyali da kuma mata masu fama da yawan ciwon mara lokacin al'ada ta karshen wata suma baa bar su a baya ba. A takaice dai AG Cera yana temakawa wajen magance cuttukka daban daban wadan ke damun mutum. Domin karin bayani ku tuntuni mu a wannan number +60167474649 ko kuma ku ziyarci shafin mu http://agnutritioninternational.com.