*_KALBIM_* _Mamuhgee_ #Zafafabiyar 1 Bismillahir Rahmanirraheem Ina rokon ALLAH Subhanahu wata'ala yanda zan fara littafin nan lafiya cikin aminci da yardarsa ya bani ikon kammalawa cikin kwanciyar hankali da nishadi tareda dacewa lfy Ni da yan uwana gabaki dayanmu.AMIN. Dan Allah ku kasance masu uzuri idan an samu kuskure ko mantuwa da makamantansu,Thank you. ******** ZADEENs HEALTH CEN/SPEACIALIST, WEDNESDAY 1:40Am Tin kafin isowan motocinsu da suka tinakaro babbar gate din asibitin securities na asibitin suka taso kusan a tare suna wangale musu gate din cikin sauri sbd irin gudun da motocin Ahalin ZADEEN's din suka tinkaro dashi wanda duk wani ma'aikacinsu yasan idan ciwon motacin suka tinkaro asibitin to Hasken idaniyar ahalin ce ba lafiya wadda kullum take cikin ciwo. Sauran securities din da basu qaraso bude kofar gate din ba kaf dinsu fitowa sukai suka tsatsaya a gate suna bin motocin guda uku da kallan girmamawa duk da tsakar dare ne tareda fatan Allah ya bata lafiya. Motocin na gama shigewa aka rufe gate din tareda taresa sbd babu wanda yake shiga ta wannan gate din a qaidarsa sai masu asibitin wanda kusan koyaushe suna hanyar zuwanta. Kafin suyi parking likitoci uku da nurses biyu suka fito ta private kofar da zata kaika kai tsaye zuwa Vip room din dayake sama gaba daya. A tare duka kofofin motocin suka bude kusan a tare duka suke fitowa babu wanda baa cikin kayan baccinsa yake ba sai DZAD(Dad Zad) wanda shine asalin Zadeens din a yanzu da babu kakansu kuma shine mahaifin marar lafiyar tasu sanye yake da jallabiya da qatuwar rigar sanyi ash sai hula sbd idan ciwon 'yar dayake gani a matsayin tasa bugawar zuciyar ya tashi saukowa yakeyi gaba daya daga billionaire din da ganinsa ma yake wuya ya koma kaman asalin uban da bayada komai agajin gaske yake nema a gurin Allah. Gadon da aka tura ta dashi ne komai nata a rufe ko fuskanta baa gani sbd kwata kwata basa bari ana ganinta sosai sai iya likitocin dake kulawa da ita sa ciwonta ne kadai suka san kamanninta sbd tsaro da tsananin rashin wasa da duk abinda ya shafeta. Suna wucewa ciki sauran familys din suka musu baya babu wanda zuciyarsa bata harbawa da damuwa, A daidai irin wannan yanayin ne ko lokacin idan suna cikinsa babu abinda bazasu iya kawarwa ba dan biyan buqatansu dan kuwa mantawa suke da komai da kowa sbd JANNAH. Securities din ZADEEN's dinne da suka iso asibitin ba tareda kayan securities dinsu a jiki ba sbd basa son asan akwai wani me mahimmanci a asibitin suka zagaye private kofar har ciki batareda alamar da zata nuna securities ne su ba. A sama kuwa suna isa aka shige da ita inda iya doctors dinne zasu shiga familyn kuwa a nan wani wadataccen palon jira dayake a tsare suka zazzauna cikin yanayi mara dadi wasunsu kuma a tsaye suna kaida kawo cikin rashin sauti ko kadan sbd rashin dadin zuciya. Mimi data fisu karfin zuciya akan lamarin Jannah din koyaushe itace ta dago idanuwanta da sukai laushi ta kalli Dzad wanda shima juyowa yayi ya kalleta da idanuwansa da sukai jajir kafin ya sauke ajiyar zuciya ahankali yana hade hannuwansa biyu sbd sanyin dayake ratsasa ko zai rage masa wanda kai tsaye zuciyarsa yake jin kaman yana zuwa zai masa illa sbd a wannan lokacin komai zai iya zama ajalinsa dan komai nasa yana gab da mutuwa idan har wani abu ya samu Jannah. Hannu Mimi ta miqa duka biyu ta dora akan nasa hannuwan tana rufe masa su tareda bude baki cikin tsananin karfin hali da jarumtar da su suke rasawa tace, "Insha Allah wannan karan zaa dace da zuciyar da zatai mata, Zaa dace,Jan Zata rayu kaman kowacce 'ya insha Allah, Jan zata zama kaman kowanne dan adam,zatai karatu me zurfi ta zama abinda kakeson ta zama insha Allah.... Rawa muryanta tafara yi karfin zuciyarta na neman karyewa dan haka tai shiru tana damqe hannuwan Dad din da dan karfi tana qasa da idanuwanta dake neman cikowa da hawaye. Dzat din sake kame hannuwanta yayi da nasa yana kasa cewa komai dan irin hakan baya magana kowa ya sani. Anny matar yayan jannah din wadda ke tsaye gefen mijinta MAHIR ZADEEN riqe da hannunsa tana kokarin kwantar masa da hankali tareda basa kwarin gwiwa dik da itama a sanyayen take sbd duk lokacinda zaa ce jannah ba lafiya a cikin matsanancin tashin hankali take duk da tasan ta riga ta tsira ta fita daga layin wainda zaa iya rabasu da zuciyar dake bugawa a kirjinsu sbd dubawa ko zata daidaita da wadda zata zaunu a kirjin wadda suke son nemowa zuciya kota halin yaya. Baro gurin Mahir tayi ta dawo gefen Mimi tayi ta zauna ahankali tareda dafata ahankali tana furta mata kalaman kwantar da hankali da fatan ranar warakar jannah taxo. Mahir zaunawa yayi shima yana dora kafarsa daya akan daya sbd sanyi da shima yake ratsashi wanda yakejin kamar fatar jikinsa ce ta bude kai tsaye sanyin na shigar masa kashi yana daskarar da jininsa gashi kayan bacci ne a jikinsa riga da wando masu tsananin taushi sbd tsadarsu sai jacket daya doro akai. SALEEM ZADEEN wanda yake bin mahir kuwa kasa zama yayi sbd kansa dayake jin kaman yana motsi dan shi sam dan zafi ne baya da hakurin suspense irin wannan kansa yakejin kaman zai zare. Shima riga da wando ne a jikinsa na bacci sedai shi hoodie jacket ce a jikinsa sai kai da kawo yakeyi yana kasa dago jajayen idanuwansa da suka sauya. Kofar palon aka turo da sauri wadda ta saka dukkaninsu dagowa suna kallan Dr AMMAR ZADEEN wanda kai tsaye ya komar da kansa baya ne yayi karatun likitan Zuciya sbd Jannah kadai. Idanuwansa da sukafi na kowannensu sauyawa ya dago ya kalli kowannensu kafin ya kalli dzat ya basa kwarin gwiwa ya juya ya fice zuwa dakin da jannah din take da doctors sbd shi biyawa yayi inda aka sanar dashi ana tinanin an samu donor kafin ya wuto nan shiyasa suka rigasa isowa. Zaman kusan awa daya zuwa biyu sukai cikin tsananin daci da damuwar zuciya kafin Ammar ya fito ya shigo dakin yana sauke numfashi me tsananin zafi da huci ya qaraso ya zauna kujeran datake kallan su Dad din ya dago idanuwansa ya kalli dad. Ajiyar zuciya me sanyi dad din ya sauke a natse yanajin hankalinsa na dawowa jikinsa take yaji dacin zuciyarsa ya ragu sbd yasan Ammar ko zuciya dubu jannah ke buqata zai nemosu ayita gwadawa har a samu wadda zatai daidai a saka mata kota halin yaya ba damuwarsu bane. Mahir ma ganin hakan ya sauke ajiyar zuciya a boye kafin ya juya ya kalli Anny da kusan itama take ta fahimci akwai wani abin kenan da ido yai mata maganar ta fita da Mimi. Ajiyar zuciya da numfashi itama ta sauke tareda dafa Mimin cikin kulawa da nuna tausayawa sosai da nutsuwa tace, "Mimi muje mu duba Jannah din doctors din sun fito" Dagowa Mimin tayi ta kalli Ammar wanda ya gyada mata kai alamar eh zasu iya zuwan, Mahir ta kalla shima ya sakar mata murmushin karfin halin alamar insha Allah jannah yanzu zata samu sauki. Miqewa tayi Anny tabi bayanta suka fice daga gurin Anny taja kofar ta rufe suka nufi dakin da jannah din take. Suna ficewa Ammar ya sauke numfashi tareda dagowa ya kalli dzad dake jiran bayaninsa ya bude baki yace "Ansamu donor wanda ta ko ina muke saka ran tayi.... Katsesa DadZad yayi da cewa "Mene ake jira to? Saleem da baida hakurin jiran komai batareda sanin abinda Ammar din zai fada ba ya matso gaban Ammar din kai tsaye yace "Indai ansamu zuciyar da zataiwa Jan ko duka tawa dukiyar dana mallaka akeso zan bayar a karbo heart din ko a inane take kawai ka tabbatarda ka amsota Jan ta sameta" Yana gama fadar haka ya juya ya nufi kofa ya fice zuwa dakinda jannah din take ya turo musu kofar da karfin daya saka dukkaninsu rintse idanuwansu banda Dad da bai motsaba har lokacin jiran sauran bayanin Ammar din yake wanda daman ba duka zance sukeyi da Saleem ba sbd zafinsa da rashin hakurinsa tareda rashin yadda da raayin kowa wani lokacin sai na kansa. Ammar takardin dake cikin aljihun jacket dinsa ya fitar ya ajiye akan table din gabansu ya mayar da bayansa jikin kujeran dayake ya jingina yafara cewa "Daya daga cikin asibitin da muka saka likitocinmu aka samo wadda zatai daidai insha Allah kuma kusan shekarunsu daya da Jannah din sedai matar Aure ce dan tanada tsohon ciki ma sedai batareda saninta ba likitocin sun duba zuciyar komai lafiya kalau." Ajiyar zuciya me tattareda samun kwanciyar hankali mahir da dad din suka sauke lokaci daya sbd abinda kawai suke son ji kenan indai komai lafiya kuma ana tinanin zatai to sauran bayanin ba damuwarsu bane sbd sai sun rabata da wannan zuciyar datake bugawa a kirjin ta sun sakawa tasu yar batareda saninta ba sbd itace kusan ta numbar da bazasu iya kirgawa ba sai an cire aga bata daceba. Dad din a natse yana komawa take Dzad dinsa ya gyara zamansa na asalin Me kudin dayake murza lokacinsa a yanzu ya kalli takardun batareda ya miqa hannunsa ya tabasu ba yace "Kawai ku saka lokacinda zaayi aikin shine abinda yakeda mahimmanci amma sauran aikin ba buqatan damuwa, Ku saka likitan datake gani acan asibitin gwamnatin ya turota nan asibitin batareda bata lokaci ba." Mahir daya miqa hannu ya dauko takardun ya bude ya zubawa sunan dayake kai idanuwansa tsawon seconds ya duba bayananta da bai fahimci komai a cikinsu ba sbd tin daga sunan da garin datake babu wanda ko a cikin wani yare ya taba ji sbd ba anan suka tashi ba bare susan sunayen garuruwa duka bare qauyuka dayake ganin kamar dabbobine kadai suke iya rayuwa a cikinsu. Jefa takardun yayi a kan table din kafin ya kalli dad din a natse yace "Inaga zaifi tinda an samu wanda zatai din and she's preg abari ayi amfani da tsufan cikin da haihuwansa" Kallansa Ammar yayi yana tinanin abinda yake fada wanda shi idan tasa zaa bi babu abinda zai tsaya jira bayan cirewa da sakawa Jan. Dad shiru yayi batareda ya kalli kowannensu ba sbd maganar mahir din dan mahir shine kusan kamar me hangen lamuransu a duk lokacinda zaayi huldan business da irin wannan mummunar ta bayan fagen shine yake aunawa da hangowa ya fada yanda zaayi kuma hakan akeyi a dace sbd yanada ilimin nutsuwar fahimtar komai da mutane, Hakama yanada wani irin ilimin dayafi duka familyn harshi dad din dan duk da dukkaninsu baa qasar suka taso ba sai yanzu ne da suka zabi dawowa gida sbd nemawa jannah kalbim. #MAMUH #ZAFAFABIYAR #MASTERPIECE #BESTSTORY #BESTLOVE #BESTROMANCE #BILLIONAIRES WAR #CRAZYLOVE #ZADEENS #LIMBAS ZAFAFA BIYAR KALBIM 500 mamuhgee A DUNIYATA 500 Huguma AJIYA A DUHU 500 Billyn Abdul KIRJIN ME HANKALI 500 Miss xoxo Pay at 0022419171 AccessBank Maryam sani gummi Shedan biya 09033181070 Or mtn vtu at 09032345899_*KALBIM*_ _Mamuhgee_ #ZafafaBiyar 2 *ZUZEAMVENTURES* 08144015291 Aslm barkanmu da wannan lokaci Ina Mai farin cikin sanar daku cewa Zuzeam ventures takawo maku ingantattun magunguna masu inganci cikin Aminci Muna da kaya kamar haka Mallaka Maganin sanyi Maganin cire tumbiMaganin farin jini Maganin matsiMaganin mata Maganin sa ni’ima da dandano Dulka Amare Set na gyran jiki Set na amarya Tabaje tsumin Gomba Xuma kiba ta hips and Brest Magungunan gyran Brest Magungunan Karin hips Maganin sliming Muna da kaya masu inganci  cikin sauki da rahusa Ina wadda keneman mallaka sahihiya quaranty wlh hajiya kixo ga zuzeam ventures xakiji ddin mallaka duk fadin ran ogah duk fadansa wlh sai yyi sanyi 08144015291 Idan maganin mata kikeso akwai Idan gyran jiki kikeso gyran fata gyran Brest magungunan sa kiba da hips DOMIN samunta Kai tsaye kira wannan no 08144015291 DOMIN mgn da ita whatapp 08144015291muna tura kayanmu ko ina cikin iKon allah 🥰👌🏻 Bononza Bononza Tsimin mangoro 1k🥭 Tsimin dabino 1k Gumba ukku balai 700 Gumba aya da nonon rakumi 700 Garin kafi ciccibi 500 Garin bata gaban kishiya 500 Matsin mallaka tada zaune tsaye 2500 Turaren mallaka ba aba mai kishiya 2500 Total kayan 9500 Za a bakisu akan 3800 Kuma mutun goman farko nadakyautar Abun 2k 🗣️🗣️🗣️🗣️🗣️🗣️ ASSALAMU ALAIKUM ALHAMDULILLAH YAN UWA  NEW PROMO YA KAMMALA💃🏽💃🏽💃🏽😁😁😁 da 5k dinki ki kwashi kayan 12k hajiyata 💃🏽💃🏽💃🏽😃🙃Kazar gadali ta mallara Rabi 3500 Tsimin gam gam 1500 Ruwan kara zunzurutun dadı😋800 Garin 7in1 1k Gumba 3 balai 500 Gumba kwakwa da dabino 500 Infection ruwan tsarki 1k Garin zunzurutun dadi 1200 Matsin ba a fira d wando 500 Matsin infection mai matse mace gam 500 12k All at 5k 08144015291  kedai dannan link dinnan don samun naki ki maza kiyi bucking koda kudinki saida Rabonki *********** Shiru dukkaninsu sukai daga dzad din har Ammar suna sake shiga nazarin maganar mahir wanda yake sake kokarin nazarta yanda zasu samu damar samun komai batareda wani damuwa ba dan shi sam baya yadda da damuwa ko tangarda a aikinsa shiyasa yake tamkar maye gurin nutsuwa ya hango ya hanga kafin ya fada. Dzad duk abinda mahir ya fada yana kokarin bada damar abi hakan sbd yafi kaf yayansa nutsuwa da bin komai a tsare amma ayau yanajin kaman hakurinsa bazai barsa ya jira lokacin da mahir din yake fada ba sbd kada su rasa zuciyar wadda ake jiran kokuma idan gurin haihuwar ta rasu fa.? Sun raba mutane da dama zuciyoyinsu sbd jannah amma babu wanda aka dace wanda ma basu san adadinsu ba ta boyayyar hanya To ayanzu da suka samu bayan tsawon lokaci ana nema kuma a tsaya jiran wani haihuwar. Mahir daya fahimci tinanin da Dad din yake sake bude baki yayi yace "Jiran haihuwarta na nufin samun dama da dalilin rasuwarta ga mutane da yan uwanta shiyasa ana buqatan a jira lokacin haihuwan tayi sbd lokacin haihuwar ya matso sosai hakan ne zai saka komai ya tafi very neat tin daga cirewa da sakawan da rufe komai". Ammar da zuciyarsa ke bugawa da sauri yana jin kansa na juyawa idanuwansa na ja jin yakeyi kaman bazai iya jiran lokacinba dan kuwa shi jinma yake kaman ya fizgo zuciyar a daren nan yazo ya sakawa Jan, Shi a yanda yakejin yana zaucewa akan ciwon jannah duk mutanen dayake gani suna yawo zai iya ringa binsu yana fasa kirjinsu yana qwato zuciyoyinsu babu ruwansa da rayuwarsu indai jannah zata rayu. Mahir ganin alaman Dad ya aminta da hakan ya sakasa kallan Ammar shi da Dad a tare sbd sanin shine mai juyewan kai idan wannan lamarin ya taso kwata kwata bayaji baya gani kawai abu daya ya sani shine karban kalbim kota waye ba ruwansa. Dad ne ya bude baki a natse yace "Ammar abari ayi hakan sbd tafiyar da komai batareda garaje ba ko dan ita jannah din hakama aikin nutsuwar da kwanciyar hankalin zaifi, Tinda aka riga aka sameta duk inda zata shiga bazata gujewa abinda yake jiranta ba sbd yanzu zuciyar Jannah ce kai tsaye take bugawa a kirjinta babu abinda zai hana jannah mallakar wannan zuciyar me bugawa." Numfashi me zafi da damuwa Ammar ya sake kafin yaji ya aminta da hakan dan haka zasu saka masu bibiyar yarinyar da bincike sosai akanta duk da babu ruwansu ba abinda ya shafesu da inda ta fito kokuma wace ita waye danginta. ******ASALIN LABARIN/SHEKARUN DA BAYA. PROF ZAHARADDEN ZAADEN shine asalin mahaifin Yayansu uku biyu maza sai mace daya wadda yayunta mazan ke tsananin kauna sbd mahaifiyarsu ta rasu a hannun matar mahaifinsu suka taso, Prof dan bokon gaske ne wanda ilimin bokon dana addinin suka shigesa sosai hakama yanada arziki sosai wanda ya dade sa barin qasar yana malaysia acan yake zaune da iyalinsa gabaki dayansu. BOUKHAR Zadeen shine babba sai MAHMOUD Zadeen tukuna qanwarsu ZAYNEB, Matar Mahaifin nasu bata taba haihuwa dashi ba dan haka su kadaine yayansa wanda suka girma kowannensu ya zama babban mutum, A malaysia suka taso acan sukai karatu sai daga baya dukkaninsu su ukun suka dawo Nigeria tareda mahaifin nasu wansa tsufa yazo masa sosai. Bayan tsawon shekaru Anyiwa Zeynab aure da wani prof itama a porthacort, BOUKHAR da MAHMOUD kuwa kowannensu na qasa daban gurin karatu, Mahmoud ya riga boukar aure kuma daga mahmoud din har zayneb babu wanda ya samu haihuwa a cikinsu har saida Boukhar yayi aure shine ya fara haihuwa a cikinsu. Familyn ZADEEN's din sunada wani irin tarin arzikin dayake da yawan gaske da basuma san ya zasuyi dashi ba, Bayan arzikin mahaifinsu prof me tarin yawa su kansu sun tara na kansu me yawan gaske dan kuwa ko Zaynab datake mace a cikinsu itama tanada nata arzikin sosai. Suna tsananin son junansu wanda hakan ya saka iyalansu ma kansu yake a matiqar hade duk da su ukun gaba daya basa qasa daya. Mahir shine babban dan Boukhar zadeen wanda ya haifesa a Greece, Bayan haihuwar Boukhar Prof ya rasu wanda hakan ya saka dukkaninsu tattarowa suka dawo Nigeria. Mahaifinsu nada kadarori sosai wanda bazasu iya gama hadasu lokaci daya ba dan haka mahmoud ne kadai ya koma boukar kuwa dole ya zauna Nigeria tareda iyalansa. Umma matar mahaifinsu wadda ta riqesu tamkar yayan data haifa ba cuta ba cutarwa hannun Boukhar ta dawo dan yayansu ma basusan cewan ba itace ta haifi iyayensu ba sbd kulawa da kaunar dake tsakaninsu ta uwa da yayanta. Mahir nada shekara biyar a duniya Zayneb ta samu ciki wanda yazo mata da matsala sosai sbd manyanci da dadewan datai bata haihun ba. Cikinta na sake gaba girman matsalarta na qaruwa wanda daga baya aka gano tanada heart diseases wanda basu taba sani ba. Hankalin familyn ya tashi sosai wanda ya sakasu dawowa da ita hannunsu aka fara neman mata lafiya. Lokacinda aka gama bincike sosai akan ciwon nata aka gano tana buqatan heart transplant maana dashen zuciya. Hankalinsu ya tashi sosai sbd ciwon nata bawai sbd zuciyar da zaa nema dinba sbd ganin sukeyi sunada dukiyar da zasu iya siyan mutum gaba dayansa su cire abinda sukeso a jikinsa. Cikinta na kaiwa wata tara suka tattara gaba daya familyn suka koma Greece sbd haihuwarta da basa fatan matsala komai kankantarta. Tin daga kan ummah da zayneb din da boukar da matarsa da mahir da mahmoud ma acan ya samesu da fmlynsa suka dawo zama. Cs akaiwa zayneb aka ciro mata Baby boy wanda Boukhar ne ya saka masa suna Ammar sbd har lokacin mijinta bai taho ba yana porthacort da matarsa daya dan haka suka suka tattara suka watsar. Tinda zayneb ta haifi Ammar bata sake lafiya ba sai ramewa takeyi tana wani irin hasken daya saka hankalin duk wanda yake familyn nasu tasu musamman yayun nata wainda suka ringa nema mata donors tako ina amma babu inda aka samu, Sassaucin da suke samu a zuciyoyinsu shine likitoci sun tabbatar musu da akwai sauran time sosai kafin zuciyar ta gaza gaba daya dan haka suka ringa zubarda dukiya qasa qasa suna neman donor. Ammar kuwa kusan Mimi ce mahaifiyar mahir matar Boukhar din ta renesa tin daga ranar da aka haifesa itace ta zama uwarsa dan ko nonon mahaifiyarsa baisha na wata biyar ba wata hudu aka ciresa daga nonon sbd bazata iyaba ta bushe sosai. Duk wannan ciwon da haihuwar mijin zayneb din baizo yaga matarsa da dansa ba sai so daya dan haka su kuma basajin zasu taba basa ita ta koma bare Ammar da sukejinsa fiyeda komai sbd tsananin kaunar da sukewa kanwarsu. Ammar tinda ya taso ya samu mahaifiyarsa a cikin mummunan hali harya fara girma a hakan yake ganinta wanda hakan ya taba zuciya da kusan lafiyarsa dan kuwa yanada qawa zucin mahaifiyarsa sosai musammam daya fahimci baida uba bayan Boukhar wanda Suke kira da Dad Zad sai Daddy mahmoud wanda takanas ya bude babbar asibiti sbd ciwon Zayneb kawai dan samun donors. Mommah zayneb tinda ta haihu ta cire rai daga rayuwa sbd yanda takejin ita kadaice ta sani a hakan tana dauriya ne sbd ragewa yan uwanta damuwa da 'danta wanda ya sakata aransa sosai fiyeda komai. Sbd ciwon zayneb Boukhar da Ammar da mahmoud saida suka koma abin tausayi duk girman arzikinsu, Ummah kuwa babu ranar da bata kuka idan ta kalli yanda zayneb ta koma, Mimi kuwa sosai itama ta tashi akan Ammar sbd saida ya zama traumatised kwata kwata baya gane karatun komai a school duk da mahir yana kokari sosai akan dan uwan nasa amma saida teachers suka gano suka bada shawarar Ammar din ya fara ganin likita. Ana cikin hakan ne Mimi ta samu ciki wanda itama ta fara shiga matsalar rashin lafiya me nauyi sbd ga cikin dayazo da ciwo ga lalurar Ammar ga kuma ta familyn da kowa yake cikin damuwa da qunci. a wannan lokacin ZAADENs suka shiga matsanancin halin damuwa da qunci, Gasu da abin duniya me tarin yawan da basa ma san menene rashi ba ko wata kalmar datai kama da hakan amma sam basa cikin farin ciki. A haka cikin Mimi ya isa haihuwa ta haifi Saleem wanda haihuwarsa ta fara dawo sa farin ciki rayuwarsu. Mahir da Ammar kusan tare suka taso kaman ba shekaru sosai tsakaninsu sbd kaunar datake tsakaninsu tafi karfi akan wadda ke tsakanin mahir din da saleem. Haihuwar saleem da shekaru biyar Allah yayiwa zayneb rasuwa bayan ta gama qarewa ta koma kamar qaramar yarinya hakama anyi mata dashen zuciyar wanda ta samu chronic rejection maana transplant failure. Rasuwar Zayneb ta girgiza duniyar ZADEEN's gaba daya ta yanda tin daga lokacin suka sauya kaman basu din ba. Ammar ya shiga sabuwar trauma wadda ta sakasu barin qasar gabaki dayanta sbd a sauya environment a bisa shawaran doctors dake dubasa. Daddy mahmoud ma barin qasar yayi kwata kwata ya koma Nigeria. Dad Zad kuwa UK ya koma da iyalinsa da ummah suka bude sabuwar rayuwa acan doctors kuma na duba lafiyar Ammar wanda kansa kamar ya tabu amma ahankali ahankali ya samu sauki harya koma karatunsa tareda yan uwansa. Hankalinsu ya kwanta rayuwarsu ta koma ta asalin jin dadi da kwanciyar hankali arzikinsu kuwa sai abinda yaketa qara yin gaba duk da ciwon rashin Zayneb yana zuciyar dadzad kwata kwata ya kasa dena jin radadin rasata hakama Ammar ya kasa cire ciwon da rashin mahaifiyarsa yabar masa duk da ya danne ya koma kaman kowanne dan adam karatu yakeyi sosai. Mahir,Ammar da saleem ZADEENs sun taso cikin wani irin gata da hutu tareda rayuwar rashin kwaba da rashin sanin mahimmanci komai da kowa bayan abinda sukeso. #MAMUH #ZADEENS #LIMBAS #BESTLOVE #BESTSTORY ##CRAZYLOVE ZAFAFA BIYAR KALBIM 500 mamuhgee A DUNIYATA 500 Huguma AJIYA A DUHU 500 Billyn Abdul KIRJIN ME HANKALI 500 Miss xoxo Pay at 0022419171 AccessBank Maryam sani gummi Shedan biya 09033181070 Or mtn vtu at 09032345899*_KALBIM_* _Mamuhgee_ #ZafafaBiyar 3 *ZUZEAMVENTURES* 08144015291 Aslm barkanmu da wannan lokaci Ina Mai farin cikin sanar daku cewa Zuzeam ventures takawo maku ingantattun magunguna masu inganci cikin Aminci Muna da kaya kamar haka Mallaka Maganin sanyi Maganin cire tumbiMaganin farin jini Maganin matsiMaganin mata Maganin sa ni’ima da dandano Dulka Amare Set na gyran jiki Set na amarya Tabaje tsumin Gomba Xuma kiba ta hips and Brest Magungunan gyran Brest Magungunan Karin hips Maganin sliming Muna da kaya masu inganci cikin sauki da rahusa Ina wadda keneman mallaka sahihiya quaranty wlh hajiya kixo ga zuzeam ventures xakiji ddin mallaka duk fadin ran ogah duk fadansa wlh sai yyi sanyi 08144015291 Idan maganin mata kikeso akwai Idan gyran jiki kikeso gyran fata gyran Brest magungunan sa kiba da hips DOMIN samunta Kai tsaye kira wannan no 08144015291 DOMIN mgn da ita whatapp 08144015291muna tura kayanmu ko ina cikin iKon allah 🥰👌🏻 Bononza Bononza Tsimin mangoro 1k🥭 Tsimin dabino 1k Gumba ukku balai 700 Gumba aya da nonon rakumi 700 Garin kafi ciccibi 500 Garin bata gaban kishiya 500 Matsin mallaka tada zaune tsaye 2500 Turaren mallaka ba aba mai kishiya 2500 Total kayan 9500 Za a bakisu akan 3800 Kuma mutun goman farko nadakyautar Abun 2k 🗣️🗣️🗣️🗣️🗣️🗣️ ASSALAMU ALAIKUM ALHAMDULILLAH YAN UWA NEW PROMO YA KAMMALA💃🏽💃🏽💃🏽😁😁😁 da 5k dinki ki kwashi kayan 12k hajiyata 💃🏽💃🏽💃🏽😃🙃Kazar gadali ta mallara Rabi 3500 Tsimin gam gam 1500 Ruwan kara zunzurutun dadı😋800 Garin 7in1 1k Gumba 3 balai 500 Gumba kwakwa da dabino 500 Infection ruwan tsarki 1k Garin zunzurutun dadi 1200 Matsin ba a fira d wando 500 Matsin infection mai matse mace gam 500 12k All at 5k kedai dannan link dinnan don samun naki ki maza kiyi bucking koda kudinki saida Rabonki *********** Mahir Zadeen shine kokarin naci akan komai saiya gano komai akan duk abinda yaga zai shiga rayuwarsa ko ta familynsa, Baya maamala da mutune ko abu ko wane iri ne kuwa batareda ya samu sanin mai zurfi akansa ba, Bayan familyn baya son kowa dan hakan ne ma baya shiga mutane sosai ko hulda dasu hakama bai yadda kowa ya kusanci fmlynsa ba sbd bai yadda da kowa ba akansu, Hakama tin kafin shekarunsa sukai ya fara shiga huldodin familynsa sbd bi da kauce duk wani abu da zai cutatar dasu ko dukiyarsu. Allah ya basa wani irin sharp kai da qwaqwalwa kamar maye dan hakan ne yasa dole da wuri su Dad suka bari ya shiga huldan duka zadeens babu wanda bai sani ba. Hakama tin daga Dzad da daddy mahmoud babu wanda yake boye masa komai sbd ganin wani sharp kaine dashi. Ammar ma yanada ilimin sosai sedai trauma dinsa tana damar masa da lissafi so da dama dan haka shi ya kasance kamar mara hankali akan abinda yakeso, Akan familynsa zai iya komai me kyau da mara kyau bai damu ba, Kaf familyn ZADEEN's babu wanda yake kallan gaskia ko adalci akan yan uwansu, Sunada wani irin son kai da basa duba komai da kowa sai kansu, Babu ruwansu da ko rai zaa rasa indai akan buqatarsu ne ko abinda suke so kuma hakan tamkar a jininsu yake dan kuwa babu wanda bazai iya komaiba a cikinsu akan abinda suke so ko buqata, Inda tsananin son zuciyarsu da son kansu yayi mugun munana shine ko dayansu yake buqatan abu to zasu hadu su samar masa da abin nan koda kuwa hakan na nufin wasu zasu shiga mummunar matsala koda kuwa ta rasa rai ce su ba damuwarsu bane. ZADEEN's sunada power me karfin gaske,sunada kudi,sunada kwarjini sunada isa,sunada duk abinda dibbin mutane da yawa ke tsananin nema da so na rayuwa basu samu ba, Duk wannan lokacin da aka dauka bayan qara habbaka da samun power babu abinda sukeyi dan hakan ne ma ya saka koda basa zama a qasarsu sunyi suna da ficen da aka sansu dan kuwa ko a Nigeria din sunada power din da ko wasu masu mulkin basuda ita. Sukan taho Nigeria din sosai dukkaninsu sedai basa wani jimawa sosai suke komawa dan hakan kan yayan yake sake budewa da gogewa a harkansu sosai. Wani cikin Mimi ta samu wanda ya saka ya saka Ammar ajiye komai ya koma kulawa da ita sbd dukkanin qawa zucin dayake dashi da mommah akan mimin ya dawo Hakama wani irin tsananin so da kaunar cikin Allah ya jarabcesa dashi wanda ya ringa rokom Allah yasa mace zaa haifa a saka mata sunan mahaifiyarsa. Yanda Ammar ya kwallafa rai akan son cikin da fatar a haifi mace ya saka kusan kowa familyn tsananin son hakanta shigesa sai gasu dukansu kaf sun qwallafa ran Wata zayneb zaa haifa. Kusan komai ajiyewa sukai suka maida kaf nutsuwarsu akan cikin dan haka Mimi ta dage da adduar Allah ya bata mace sbd samunta shine hasken dazai qara cike rayuwar zadeens da suka kasa manta radadin rashin zayneb. Yanda kaf familyn suka duqufa da rokon samun Zayneb suka manta da komai zaka roqa ka roqi me albarka ko kuma zabin mafin alkhairi, Ita haihuwa sam ba sai wanda kakesoba Duk wanda Allah ya baka ka roki me albarka kawai kokuma lafiyayye. Tin daga kan ummah datake tsohuwarsu har kan duk wanda yake familyn Allah suka ringa roqo akan zayneb sukeso kota yayane Allah ya basu wata zayneb din da suka rasa. Hankalin Mimi fara tashi yayi ganin yanda duka hankalinsu ya gushe ko yayane so suke Allah ya karbi Addua da fatansu. Damuwa da tsoro ya saka naquda zuwar mata batareda cikin ya isa haihuwa ba dan haka suka dunguma asibiti. Ko asibitin da aka kaita babu me zuwanta sai wanda yakeda matsayi da kudin da kusan koina ka san dashi dan haka tin tana ciki aka fara yada ZADEEN's na shirin welcoming sabuwar princess din familyn. Tsaron asibitin kadai zakasan masu abin duniya ne a asibitin dan haka Kusan su kadai ne a asibitin ranar. Naquda sosai Mimi tayi kafin Allah ya bata ikon haihuwar abinda suka roka 'Ya mace Kyakkyawa da ita fara tas kuma kusan kammanin mommah zayneb din ta dauko dan kusan familyn kamanninsu daya shiyasa suke da wani irin kyau da kwarjini dukkaninsu tin daga kan su dzad din. Tin a asibitin Dad ya saka mata sunan ZAYNEB BOUKHAR ZADEEN bayan ya dauketa da hannuwansa yanajin soyayyarta da kaunarta fiyeda duka sauran yayan daya haifa sbd tsananin kaunarsa ga zayneb da suka rasa. Mahir ma jin yayi tafi masa duk abinda suka mallaka dan haka ya rungumeta sosai yana addua. Saleem kuwa take yaji zai iya komai akanta. Ammar ne na karshe a daukanta sbd idanuwansa da suka ciko da hawaye zuciyarsa na harbawa da wani irin tsananin kaunarta dan fuskan mommansa kawai yake gani akan nata ga kuma sunan da Dad ya ambaceta dashi na mommansa. Ahankali ya rungumeta a kirjinsa hawayen dake idanuwansa na gangarowa ya bude baki Ahankali yace "JANNAH" Tausayinsa me tsananin gaske ne ya rufe Mimi ta miqa masa hannu tana kokarin boye nata hawayen sbd rasuwar momman data dawo musu sabuwa. A sanyaye ya qaraso gurinta ta nuna masa gefenta ya zauna ahankali yana kama hannunta daya datake miqa masa ta dan kwanta gefen jikinsa tana cewa "Ka samu jannah" Murmushi yayi yana zubawa fuskan babyn idanuwansa tana baccinta hankali kwance kamar ba rai a jikinta. Saida Mimin ta kwana asibiti kafin aka sallamesu suka koma gida cikeda farin cikin da suka manta rabonsu da irinsa. Haihuwar Jannah zadeens itace babban Farin cikin daya cike gaba daya rayuwar ahalin gabaki dayanta dama duk wanda yake muaamala da huldan business dasu, Duk wanda yake aiki a karkashinsu ma yayi farin cikin samun jannah sbd tayasu farin ciki dan haka tin tana jaririyarta duniya tasan da irin tsananin son da Ake mata, Duniya ta sheda jannah zadeen itace hasken idaniya da rayuwar ZADEEN's. Rayuwarsu ta dawo kamar sabuwar duniya da suke barewa a leda yanzu, A baya komai ma wasa ne a yanzu ne ZADEEN's ke sake zamowa ZADEEN's da kowa yake shakka gashi daddy mahmoud ma ya dawo da familynsa sun hade sun sake bunqasar datake bawa mutane tsoronsu amma har lokacin matarsa shi bata haihuba amma bai wani damuba sbd yayan 'dan uwansa da Ammar dan zayneb sun ishesa. *******A DAYA BANGERN KUWA CAN BAYA. Kauyen Bondi Ruwa akeyi sosai tsakiyar dare guraren karfe daya da rabi gari yayi tsit babu kowa babu komai bayan ruwan da suke sauka sosai da karfi. Qaramin gidan ne sosai wanda rabinsa yake a zube katangar ruwa ya zubar tintini. Dayan bangaren da bai fadi ba daki daya ne sai qaramin ban daki wanda shima rabinsa ya zube buhu ne a rufe da rabin, A cikin dakin macen datake kwance tana hada wani irin zufa me tsananin gaske duk da sanyin ruwan da akeyi yana zubowa cikin dakin daga sama sbd gefe daya langa langar dakin ya bude. Dan ta dake gefenta idanuwansa sunyi jajir sbd tsananin dacin ganin mahaifiyar tasa a hakan. Tsohon cikin dayake jikinta ya kalla idanuwansa suka sake kadawa sbd damuwa da dacin a halinda mahaifiyarsa zata haifo masa kaninsa ko kanwarsa. Hannuwansa ya miqa ahankali ya janyo zanin da bayada sanyi ya rufawa Umman tasa ya bude bakinsa da muryansa me sanyi yace "Umma sannu" Kasa magana tayi sbd wani tsananin azababben ciwon marar daya taso mata tanaji jini na balle mata amma ta danne cikin tsananin azabar da bata taba jinta ba sbd batason daga hankalin 'danta dayake shi kadai hasken rayuwarta da batada kowa sai shi hakama batason ya gani ya duk da tasan duk ayita a qare shine zai tayata haihuwar kila tinda batada me taimakonta a rayuwar nan yanxu bayan shi data haifa. Daqyar ta iya bude idanuwanta da sukai tsananin nauyi ta kalli farar fuskansa ta asalin fulani da dasashiyar murya tace "ABDULAZIZ" kasa dagowa yayi ya kalleta sbd hawayen da suka ciko idanuwansa yanajin duk duniya babu abinda ya tsana kamar dangin mahaifinsa da suka kasa taimakon mahifiyarsa bayan rasuwar mahaifinsu. Numfashi take kokarin saukewa cikin azaba sbd sanin taurin zuciya irin ta ABDULAZIZ har abada bazai taba so da kaunar ko mutum daya a cikin dangin mahaifinsa ba dan duk da abinda ya tsana da gaske yake tsanarsa. Jini ne ruwan dayake zubo musu ya gangaro daga karkashin Umman. Jajayen idanuwansa ya dago cikin duhun daren zaiyi magana sai kawai umman ta masa wata irin riqo me qarfin gaske tana rintse idanuwanta cikin azabar gaske tayi wani irin nishi take ta haifo abinda yake cikinta. Hawayen azabar ne suka gangaro musu shida umman a tare sbd irin riqon datai masa amma jin kukan jaririyar ya sakasa bude idanuwansa duk da baya ganin komai sosai ya sunkuyar da kai yana Godewa Allah cikin hawaye duk da ba wasu shekaru ne dashi ba sosai iyakacinsa shekaru goma sha hudu. Batason abinda zai saka Abdul din yasan meyake wakana dan haka ta dade da tanadar rezanta dan haka da kanta ta yanke cibiyar ta dauki yar hannunta na rawa da hannu ta shafa gabanta taji mace ce dan haka yaye zanin daya rufa mata ta saka yar a ciki ta miqa masa tana numfashi daqyar sbd jinin dayake neman bugar da ita. Hannuwansa rawa sukeyi sosai ya karbeta tana bude idanuwansa sosai a cikin duhun dan yaga halinda umman take ciki amma baya ganin komai. Shiru dakin ya sake dauka yana rungume da yar yana jin wani irin tsananin so da kaunarta da yakejin ko rayuwarsa zai iya badawa dan bata kariya itada ummansa. Kanwarsa ce uwa daya ta haifesa hakama daga tsotsan uba daya suka fito kuma batada kowa bayan shi da umman, Hakama ummansa batada kowa sai shi, Shine zai zama gatanta itada umma koda kuwa zai rasa ransa to tabbasa zaiyi gwagwarmaya dan inganta rayuwar su biyun nan. Guraren asuba ruwan saman ya dauke dan haka ya ciro yarinyar daga jikinsa ya kwantar gefen umman ya fita cikin duhun ya nufi can karshen kauyen gurin macen da ita kadaice aminyar mahaifiyarsa duk kauyen kuma ita kadai take taimaka musu. #MAMUH #AZIZ AY LIMBA #BESTLOVE #BESTSTORY #HEARTTRANSPLANT #JANNAH ZADEENS #UMMITA LIMBA ZAFAFA BIYAR KALBIM 500 mamuhgee A DUNIYATA 500 Huguma AJIYA A DUHU 500 Billyn Abdul KIRJIN ME HANKALI 500 Miss xoxo Pay at 0022419171 AccessBank Maryam sani gummi Shedan biya 09033181070 Or mtn vtu at 09032345899 *_KALBIM_* _Mamuhgee_ #ZafafaBiyar 4 *ZUZEAMVENTURES* 08144015291 Aslm barkanmu da wannan lokaci Ina Mai farin cikin sanar daku cewa Zuzeam ventures takawo maku ingantattun magunguna masu inganci cikin Aminci Muna da kaya kamar haka Mallaka Maganin sanyi Maganin cire tumbiMaganin farin jini Maganin matsiMaganin mata Maganin sa ni’ima da dandano Dulka Amare Set na gyran jiki Set na amarya Tabaje tsumin Gomba Xuma kiba ta hips and Brest Magungunan gyran Brest Magungunan Karin hips Maganin sliming Muna da kaya masu inganci cikin sauki da rahusa Ina wadda keneman mallaka sahihiya quaranty wlh hajiya kixo ga zuzeam ventures xakiji ddin mallaka duk fadin ran ogah duk fadansa wlh sai yyi sanyi 08144015291 Idan maganin mata kikeso akwai Idan gyran jiki kikeso gyran fata gyran Brest magungunan sa kiba da hips DOMIN samunta Kai tsaye kira wannan no 08144015291 DOMIN mgn da ita whatapp 08144015291muna tura kayanmu ko ina cikin iKon allah 🥰👌🏻 Bononza Bononza Tsimin mangoro 1k🥭 Tsimin dabino 1k Gumba ukku balai 700 Gumba aya da nonon rakumi 700 Garin kafi ciccibi 500 Garin bata gaban kishiya 500 Matsin mallaka tada zaune tsaye 2500 Turaren mallaka ba aba mai kishiya 2500 Total kayan 9500 Za a bakisu akan 3800 Kuma mutun goman farko nadakyautar Abun 2k 🗣️🗣️🗣️🗣️🗣️🗣️ ASSALAMU ALAIKUM ALHAMDULILLAH YAN UWA NEW PROMO YA KAMMALA💃🏽💃🏽💃🏽😁😁😁 da 5k dinki ki kwashi kayan 12k hajiyata 💃🏽💃🏽💃🏽😃🙃Kazar gadali ta mallara Rabi 3500 Tsimin gam gam 1500 Ruwan kara zunzurutun dadı😋800 Garin 7in1 1k Gumba 3 balai 500 Gumba kwakwa da dabino 500 Infection ruwan tsarki 1k Garin zunzurutun dadi 1200 Matsin ba a fira d wando 500 Matsin infection mai matse mace gam 500 12k All at 5k kedai dannan link dinnan don samun naki ki maza kiyi bucking koda kudinki saida Rabonki ************* Duk duhu da tsit din daren baitaba jin tsoronsu ba dan a haka ya taso komai dare haka yake ratsasa gurin nemowa ummansa Abincin da zata sakawa cikinta sbd ita da babyn datake cikinta su rayu. Tafiya yayi mai nisa kafin ya isa gidan da zashi din, Kofar gidan ya tsaya idanuwansa da sukai jajir ya dago ya kalli kofar gidan yana jin zuciyarsa na quna sbd baida ikon buga kofar bisa ga dokar mai gidan, Ya saba komai dare haka yake zuwa ya buga kofar gidan idan mahaifiyarsa bata lafiya sbd Mama Sakina taje ta taimaka mata, Mama sakina kuwa komai dare yaxo ya buqaceta bata taba fashin xuwa komai fadan da mijinta zaiyi kuwa, Duk masifarsa da tsanar da yayiwa Abdul din da mahaifiyarsa sbd sun hanasa kwanciyar hankali da masifar rayuwarsu amma hakan bai taba saka sakina janyewa daga garesu ba sbd kauna ce sosai a tsakaninta da Fatimar da bazata iya barinta a mummunan halinda take ciki ba itada Abdul. Ba so daya ba mijinta ya saba yiwa Abdul din dukan tsiya sosai akan zuwar masa gida tsakiyar dare. Zafafan hawaye ne suka cika idanuwansa yana kallan kofar gidan kaman zuciyarsa zata fashe da ciwo da radadin bazai iya kiran Mama sakinar ba dan yana taba kofar gidan baba ilan dukan da bazai iya bawa ummansa kulawa ba a yanzu datake tsananin buqatansa zai masa shikuma bazai iya barin komai ya samesaba a yanzu dayake son kulawa da umman da 'yar data haifo musu. Gefen kofar gidan ya koma kadan ahankali ya durqusa yana sunkuyar da kansa qasa dan jiran ayi kiran asubar da yasan lokaci yayi insha Allah. Wani irin sanyi ake kadawa sosai Sauran ruwan da aka dan dauke suna yayyafowa akansa ahankali suna ratsasa amma bai ko matsaba bare alamar tashi bakin kofar gidan. Jiran kusan awa daya da mintina yayi kafin masallaci daya kwal dayake kauyen suka rangada kiran sallan daya sakasa miqewa da dauri kafafunsa da sukai wani irin riqewa suka kasa daukansa ya zube a gurin cikin ruwa da lakar datake lalace sosai da kofar gidan. Rintse idanuwansa yayi zuciyarsa data fara bushewa tin yana karamin nasa ta masa wani irin nauyi yana jin kirjinsa na masa ciwo. Hawaye masu dumi ne suka gangaro masa ya dafa yana kokarin miqewa aka bude kofar gidan. Baba ila ne da babban dansa dayake uztaz wanda shi yake sako uban nasa gaba zuwa masallaci lokutan asuba a gida yake sallan baya zuwa masallaci da asuba. Bude kananun idanuwansa masu kama da kamar an kashe kwarkwata ya waresu akan Abdul din duk da akwai duhu sosai har lokacin amma baya buqatan wahalarda kansa gurin sanin waye dan kai tsaye yasan baida tsohon dan iskan dazai zuwar masa gida bayan Abdul din wanda yake fatar Allah ya nuna masa sunbi duniya sunbar kauyen ko gidansa zai huta da maitar Abdul din. Cikin zafin rai ya harbi Abdul din da kafarsa yana cewa "Uban waye a kafar gidana cikin duhun nan?? Cikinsa daya harba ya dafe da hannunsa daya yana dagowa cikin tsananin azaba ya dafa hannunsa daya ya miqe yana kokarin bude baki zaiyi magana Baba ilan ya rigasa da cewa "Nace uban waye ne a gurin? Gali dayake gefen baban fitilar hannunsa ya kunna yana haske Abdul din da ita cikeda mamakin ganinsa duk da yasan yana zuwan amma a cikin ruwa da sanyin nan me yakeyi a kofar gidan wanda da alama ya dan jima. Wasu hawayen ne suka sake gangarowa daga jajayen idanuwansa kafin ya bude bakinsa muryansa a sanqare da sanyi duk da yasan suna sane da waye din amma bude baki yayi yace "Nine Abdul" Katsesa Gali yayi da cewa "Lafiya kuwa cikin sanyin? Bude baki yayi zaiyi magana amma Galin ya wuce cikim sauri yayi masallaci sbd jin angama kiran. Baba ila ne ya kallesa cikeda baqin ciki da tsana me tsananin gaske yace "Allah ya tsinewa sanayyar datake tsakanin Sakina da Uwarka dan kuwa babu abinda kuke qararta dashi sai baqin talauci da baqaqen masifun da kuke yawo dashi, Ace har tsakar dare bata huta da masifunku ba, Yanzu ubanme zatai muku da asubar farin?? Wani abu me daci da nauyi Abdul ya hadiye kafin ya bude baki yace "Haihuwa ummana tayi" Cikin sabon baqin cikin daya tirniqe baba ilan ya tsaki tsokin daya saka Abdul din rintse idanuwansa yace "An haifowa sakina wata sabuwar Masifar kenan,to wlh tallahi baa gidana ba, Na gaji bazan iya ba,duk yanda nake shan rantsuwa da masifa sakina ta ture bata ji bata gani saita ringa daukan abincin danake wahala ina nemowa na gidana ta baku to daga yau ankai karshe sbd bazai yiyu ni ban tara nawa yaran dazan ringa ciyarwa ba haka kawai na koma ciyar da 'yayan wani katan" Juyawa yayi ya koma ciki yana fasa zuwa masallacin bakinsa na cikowa da kumfan masifa sbd yasan yana tafiya wlh sai an dauki abincin gidansa ko wani abin antafi dashi sbd sakina dai sedai ya barwa fatima da 'danta dan bazata iya rabuwa dasu ba. Abdul cikin tsananin sanyi da azabar data gama shigarsa ya bi bayan baban da sauri dan kada ya hanasa ma shiga. Kai tsaye dakin sakina ya nufa ya kiran sunanta cikin tsananin baqin ciki da masifa taresa bacin rai yana cewa maza ta fito. Daman ba wani nauyin bacci ne da ita ba dan haka cikin bacci taji yana kiran sunanta da karfi ta bude idanuwanta tana kokarin tashi zaune ya shigo dakin sbd daman baa dakinta ya kwana ba ranar a dakin uwargidansa ya kwana. Yana shigowa dakin ta lalubo fitilarta ta kunna haske ya wadata dakin, Akan Abdul dayake tsaye a kofa bai qarasa shigowaba idanuwanta suka sauka. Faduwa gabanta yayi da sauri ta janyo dankwali tana daurawa akanta ta miqe daga katifar datake kai tana ambatar sunansa baba ila ya katseta da cewa "Ayau idan har kika fita gidan nan kika bi yaron nan gurin uwarsa wlh tallahi a bakin aurenki hakama abinci na ko wani abin dayake nawa a gidan nan kika basu shima a bakin aurenki, Bazan iya ba na gaji da renan 'da da uwar da banda hadi komai dasu bare yanxu wata wahalar da aka sake haifowa...... Da sauri sakina ta dago idanuwanta da ciko da hawayen tashin hankali da firgicin maganarsa ta farko ta kalli Abdul jin maganar haihuwar. Shima dago jajayen idanuwansa yayi ya kalleta cikeda girgiza da tsoron abinda Baba ilan ya fada. Gangarowa hawayensa masu tsananin zafi sukai ya dan ja baya ahankali batareda ya iya cigaba da tsayawa ba sbd bai san me zai fadawa mama sakinan ba kuma. Bude baki tayi ahankali tace "ABDULAZIZ" Cak ya tsaya batareda ya dagoba. Kofar inda kayanta suke tai batareda ta cewa baba ilan komaiba, Zannuwan kayanta na sakawa masu tsafta ta dauko tareda guda biyu da rigarta ta sanyi daya da ita kadai takeda ita ta dauko wanda itace da kanta ta siya abinta da yan kudinta. Inda take ajiye kudi ta duba tana saka hannu cikin kofin silver me murfi taji babu komai a ciki. Juyawa tayi ta duba gurin ajiyarta daya taga dari bakwai ne kadai da ita dan haka ta dauko dari biyar ta juyo ta nufi kofar ta fito. Kayan ta miqa masa cikeda kunyarsa duk da yana qaramin yaro ta bude baki asanyaye tace "Ka siya mata koko me zafi sauran canjin ka siya itace ka dafa mata ruwan zafi tayi wanka itace da abinda aka haifa" Hawayensa ne suka gangaro ahankali suka sauka akan dari biyar din data dora masa a tafin hannunsa. Kasa magana yayi kai ya gyada mata ahankali yana damqe kayan hannuwansa na qara daukan sanyi. Baba ila daya kasa motsawa sbd baqin ciki da mamaki kallanta yayi ita kuma taqi kallansa Baqin ciki sake rufesa yayi kamar zai fashe sbd baqin ciki yace "Sbd ki nunamun ban isaba shine a gaban nawa ko matsawa daga inda nai maganar banba zaki dauki abubuwa ki basu?? To meye amfani na a rayuwarki sakina tinda kinada Fatima da 'danta ai saiki fice ki bisu kije na bar musu ke wlh" Abdul kafafuwansa da sanyi yayiwa mugun shiga ya ja ahankali yabar gurin yana qanwame kayan data basa da kudin. Yana ficewa gidan Mama sakina ta dago ta kalli baba ila har zatai magana sai ya katseta cikin tsananin zafi da cewa "Wlh tallahi na barwa fatima ke kawai ki tattara ki bar mun gidana ki bita can saiki kwasheta kiyi kauyenku da ita da 'yayanta" Kofa ya nufa yana ball da butarta dake hanyarsa ta wucewa yana jin zuciyarsa na wata irin tafasa da bacin rai me tsanani. Numfashi me sanyi da mutuwar jiki ta sake tana danne zuciyarta akan furucinsa wanda shedan ke ingizata data bar masa gidan nasa ta tafin sbd su fatima sunfi buqatarta amma kuma girman auren nata take kalla ta danne zafi da bacin da ranta yayi dan yanzu ne zata biye masa suyita masifa a cikin gidan har wayewar gari da wuni zasu iya wuni suna masifa. Butarta dayayi wurgi da ita ta nufa ta dauka tana qarasa zubar da ruwan ciki da suka rage ta nufi gurin diban wasu ruwan tana duba butar idan bai fasa mata ita ba. Tana diban ruwan bandaki ta fara shiga tana fitowa tai alwala ta shige dakinta. #MAMUH #ZADEENS #LIMBAS ZAFAFA BIYAR KALBIM 500 mamuhgee A DUNIYATA 500 Huguma AJIYA A DUHU 500 Billyn Abdul KIRJIN ME HANKALI 500 Miss xoxo Pay at 0022419171 AccessBank Maryam sani gummi Shedan biya 09033181070 Or mtn vtu at 09032345899*_KALBIM_* _Mamuhgee_ #ZafafaBiyar 5 *ZUZEAMVENTURES* 08144015291 Aslm barkanmu da wannan lokaci Ina Mai farin cikin sanar daku cewa Zuzeam ventures takawo maku ingantattun magunguna masu inganci cikin Aminci Muna da kaya kamar haka Mallaka Maganin sanyi Maganin cire tumbiMaganin farin jini Maganin matsiMaganin mata Maganin sa ni’ima da dandano Dulka Amare Set na gyran jiki Set na amarya Tabaje tsumin Gomba Xuma kiba ta hips and Brest Magungunan gyran Brest Magungunan Karin hips Maganin sliming Muna da kaya masu inganci cikin sauki da rahusa Ina wadda keneman mallaka sahihiya quaranty wlh hajiya kixo ga zuzeam ventures xakiji ddin mallaka duk fadin ran ogah duk fadansa wlh sai yyi sanyi 08144015291 Idan maganin mata kikeso akwai Idan gyran jiki kikeso gyran fata gyran Brest magungunan sa kiba da hips DOMIN samunta Kai tsaye kira wannan no 08144015291 DOMIN mgn da ita whatapp 08144015291muna tura kayanmu ko ina cikin iKon allah 🥰👌🏻 Bononza Bononza Tsimin mangoro 1k🥭 Tsimin dabino 1k Gumba ukku balai 700 Gumba aya da nonon rakumi 700 Garin kafi ciccibi 500 Garin bata gaban kishiya 500 Matsin mallaka tada zaune tsaye 2500 Turaren mallaka ba aba mai kishiya 2500 Total kayan 9500 Za a bakisu akan 3800 Kuma mutun goman farko nadakyautar Abun 2k 🗣️🗣️🗣️🗣️🗣️🗣️ ASSALAMU ALAIKUM ALHAMDULILLAH YAN UWA NEW PROMO YA KAMMALA💃🏽💃🏽💃🏽😁😁😁 da 5k dinki ki kwashi kayan 12k hajiyata 💃🏽💃🏽💃🏽😃🙃Kazar gadali ta mallara Rabi 3500 Tsimin gam gam 1500 Ruwan kara zunzurutun dadı😋800 Garin 7in1 1k Gumba 3 balai 500 Gumba kwakwa da dabino 500 Infection ruwan tsarki 1k Garin zunzurutun dadi 1200 Matsin ba a fira d wando 500 Matsin infection mai matse mace gam 500 12k All at 5k kedai dannan link dinnan don samun naki ki maza kiyi bucking koda kudinki saida Rabonki ************ Abdul kuwa yana fita gidan tafiya me dan tsayi yayi kafin ya durkushe a gurin yana fasa wani irin kuka me tsananin gaske sanyin gaske na ratsatsa. Saida aka fito masallaci kafin ya daure ya qarasa gida, Koda ya isa zanin dayake rufe da umman me sanyi kawai ya yaye mata ya rufa mata daya daga cikin wanda mama sakina ta basa, Leqa babyn datake kwance gefen umman yayi yaga bacci takeyi lafiya kalau dan haka ya fice. Alwala yayi ya dawo daga kofar dakin ya samu inda yayi sallah. Yana idarwa ya dawo cikin dakin ya taba ummansa yaga tana numfashi. Ajiyar zuciya me tsananin sanyi ya sauke kafin ya fita sbd gari ya waye sosai. Gurin me siyarda koko ya tafi Sai alokacin ma take hada wutar hada kokon dan haka yabar kudinsa ya koma ya nufi daji ya samo abinda zai hura wutan ruwan zafin da mama sakina tace. Duka sun jiqe abubuwan daya tsinto amma hakanan yaje ya siyo ashana ya karbo kokon daga nan ya kawo mata. Daqyar ya iya taimakawa umman ta tashi zaune ya dora mata robar kokon wadda ta bude bakinta daqyar kokon na shiga wanda zafinsa ya sakata jin hanjinta da suka nade suka dunqule fara warwarewa harma cikin na dan mata ciwo. Tana gama shanye kokon amai ya taso mata gabaki daya ta amayar dashi. Wutar ya hau hurawa wadda ta cinye gaba daya ashanar daya siyo sai daya koma ya qaro wata itama saida ta kusa qarew kafin wutar ta kama jikinsa na rawa ya dora ruwan. Hura wutar ya zauna yanayi sosai batareda ya hutaba har saida ruwan sikai zafi sosai. Umman daqyar ta iya tasowa ta nufi bandaki yakai mata ruwan shima ya fito ya dauko babyn ya fito daga daki sai a lokacin ya zuba mata idanuwansa yafara yi mata wani irin kallan tsafta me hade da wata irin kauna me tsananin gasken da batada sirki. Wanka sosai umman tayi ta gyaro kanta ta fito har lokacin bata iya ko tsayuwar kirki. Uwar haihuwar data bari a dakin ta shiga ta dauko ta goma gefen gidansu daya zube ta binneta daqyar jikin yana kakkarwa sosai sbd jirin gaske ma take gani. Yana ganin hakan ya shiga dakin da sauri ya dan gyarosa ya share ya goge duk sanyin dakin tas ya sake shimfida mata wani zanin akan qaramar katifarsu umman ta kwanta. Fita yayi ya sake siyo mata koko da saura Canjin daya rage ya kawo mata sedai koda ya dawo gabaki daya ta fice hayyacinta bama zata iya ko motsawa ba bare sanin meyake fada. Ajiye robar hannunsa yayi yana kokarin dagota amma gaba daya jikinta ya sake. Ambatar sunanta yafara yana shafa fuskanta zuwa wuyanta kuka na zuwar masa sosai. Kuka me qarfin gaske babyn datake gefensu ta fasa wanda ya sakasa saurin juyowa yana rasa ya zaiyi. Kuka sosai baby tafara wanda ya sakasa sakin umman ya zauna tsakiyarsu yana sunkuyar da kai shima ya fara kuka yana wani sheshekan da har jikinsa rawa yakeyi. Ya jima a hakan batareda yasan me zaiyiba har babyn ta gaji tayi shiru ta koma bacci. Ummansa kuwa wata firgita ta fara tana jijjiga. Qanqameta yayi yana ambatar sunanta amma batasan ma yanayi ba. Kusan awa daya a hakan kafin jikinta ya sake sakewa tayi baccin wahala. Shima a gurin cikin jikinta baccin walaha da yunwa ya daukesa. Sai azahar ya farka ya fita gidan ya nufi gurin aikin lakar dayake zuwa yana dan tayasu suna basa nera dari. Acan yayi sallah yayita musu aiki har wanda yafi karfin shekarunsa. Daga can wani kokon ya sake siyowa ya kawo yasha shida umman wadda sedai ya bata daga kwancen dan bata iya tashi hakama gabaki daya ta koma kamar ba umman tasa ba sbd wasu abubuwa takeyi da fizge fizge da zabura. Yamma nayi yasan baba ila baya gida dan haka ya dauke babyn ya rufeta da zani kusan uku ya nufi gidan mama sakina da ita sbd tanada kuka. Harya isa gidan babu wanda ya taresa ya tambayesa sbd gudunsu ma akeyi a kauyen sbd camfa ummansa da akai da baqar mace. Mama sakin wuni tayi cikin damuwa da tinaninsu dan haka tana zaune tana hada saka da warwara tagansa ya shigo da zani kallo daya tai masa ta gane jaririyarce ya dauko. Cikeda mamaki da tsoro ta kallesa tana miqewa ta karbi 'yar tana cewa "Abdul meyasa ka fito da ita?? Yaya ummanku? Ya jikinta? Kasancewarsa mara hayaniya da rashin sabo da magana sosai sbd baida abokan wasa ko wasu yan uwan daya taso cikin gata yasa ita kadaice ma wacce yake magana da ita sosaima Ya dan dago kansa batareda ya kalleta ba yace "Tanata kuka ne tin dasafe, Umma kuma batada lafiya tanata firgita" Kasa cewa sakina tayi ta nufi daki takai yar da sauri tana fitowa ruwan zafi tafara dorawa kafin ta dauko abincinta na rana da bata samu ci ba sbd damuwa ta miqa masa tace "Maza zauna ka cinye yanzu" Zaunawa yayi yaci abincin ita kuma tana sauke ruwan dauko babyn tayi tahau yi mata wanka sbd batason baba ila ya dawo ya taddasu hakama batason yayi dare a hanya da 'yar. Wanka sosai me kyau tayi mata duk da bata taba haihuwaba batasan yaya akeyiba amma dayake anata haihuwa a gidan tana gani kuka tana dan saka hannu sai ta iya. Tana gama mata wanka kayan data siya guda daya na jiran haihuwar matar Gali 'dan mijinta ta dauko ta sakawa yar ta dauko madarar shanun datake da ita me kyau ta bata kuma cikin ikon Allah yarinyar tasha take ta koma bacci abinta. Sake nade masa ita tayi sosai ta basa tace maza ya koma. Karbanta yayi ya juya ya fice daga gidan. Koda ya isa gida ummansu ta tashi tana zaune ta zubawa kofa idanuwanta da sukai fari fes hakama bakinta ya bushe sosai. Cikeda mamaki da dan farin cikin ganin ta tashi ya qaraso yana cewa "Umma kin samu lafiya? Juyo idanuwanta da suke kamar a buge tayi ta zuba masa batareda tace komaiba sbd kamar ba yayanta bane take gani. Sake tambayarta yayi yaga ko kyaftawa idanuwanta basayi kallansu takeyi numfashinta baya fitama daidai. Babyn ya bude daga zaninta ya dora mata a hannunta yana cewa "Mama sakina tai mata wanka ta saka mata kaya" Babyn ta saukar da idanuwanta ta zubawa ido tsawon mintina kafin ta dago ta zubawa Abdul din idanuwan shima Shima ita yake kallan cikin tsoron irin kallan datake musun. Sakin babyn tayi da sauri ya tare tareda daukanta ya ajiye gefensu yana cewa "Umma kin gaji ne? Har lokacin batace komaiba bata kuma dena kallansaba kaman wanda bata saniba ko bata taba ganiva. Zamewa tayi ta koma ta kwanta tareda zubawa babyn gabanta ido. Har dare yai suka kwanta batareda sun samu abinda zasu ci ba umman batai magana ba har lokacin hakama bata dena kallansu ba. Cikin tsakar dare cikin bacci yaji motsin umman ya bude idanuwansa sai yaga ta tashi zata fita ko dan kwali babu a kanta hakama bata ko iya tsayuwa da kyau. Kasa daukanta kafafunta sukai ta zube qasa kanta na buguwa da bangon kofar fita dakin take goshinta ya fashe da jini. Tashi yayi da sauri yana riqota cikin tsoro da tashin hankali yana cewa "Umma ina zaki? Zaki bandaki ne? Kallansa ta juyo tanayi kafin ta dago hannunta dayake wani irin rawa ta nuna masa kofa batareda tace komaiba. Kofar ya kalla kafin ya kalleta sai ya rasa me zai fada ya kamo hannunta kawai ya dawo da ita kuma ta biyosa kamar yarinya qarama. Kwantawa suka koma sukai take kuma saita koma baccinta. Gari na wayewa yaje yayo aikinsa ya dawo mata da koko ya sake dafa mata ruwa ya sake ficewa. Sai yamma ya dawo musu da tuwon dawa da miyar kuka dan kadan wanda aikin wahala yayi ya samosa. Kasa cin abincin umman tayi duk yanda yayi sa ita dan haka kaman yanda yake bata koko haka ya zauna ya bata abincin a baki da kansa. Babyn kuwa sake kaita yayi gurin mama sakina ta bata irin madaran jiya tasha ya dawo da ita gida. Yana dawowa a hanya ya hadu da ummansa tana tafiya tana jiri ba dankwali akanta, Da sauri ya kama hannunta suka juya gida yana mamakin abinda ya samu umman ga jikinta duk jini. Suna komawa gida ya zaunar sa ita yana mata magana amma kwata kwata batacewa komai kallansa kawai takeyi. Hawaye ya fara batareda yasan me zaiyiba. Da daddaren ranar ma so biyu tana kokarin fita yana dawowa da ita tim anan ya fahimci ummansa ta kamu da wani sabon rashin lafiyar. Kuka ya ringa yi har safe kuma da safen ma daqyar ya iya fita yabarta. Koda ya dawo bata fita ba amma tana zaune babyn nata kuka sosai kamar bataji sai kallanta takeyi idanuwanta sunyi jajir kamar zasu fashe. Daukan babyn yayi ya zauna gaban umman ya fada jikinta yana fasa kuka shima yana ambatar sunanta. Kukansa ne ya saka wani irin hawaye masu tsananin zafi da ciwon da bata saniba tsinke mata tana qanqamesa tana jin tsananin sonsa shi kadai dan shi kadai take jin sonsa amma babyn kwata kwata kamar bata santaba dan kanta dake kokarin juyewa koma ya juyen. Sun jima a hakan suna kuka duka su ukun harda babyn da suka matse a tsakiyarsu. Sun jima a hakan kafin umman tayi bacci da babyn shi kuma ya fita sallan magrib yana dawowa a gida yayi ishai sukai baccinsu. ***kwanaki suka fara tafiyar musu ahankali ahankali ya fahimta da kyau kamar ummansa ta haukace sedai hauka bame tashin hankali ba wanda asalin yunwa da infection ne daya mummunan shigarta a gurin haihuwar me mugun karfi daya juyar mata da kai kwata kwata ta manta wai haihuwa tayi. Mama sakina na cikin tsananin damuwa da tashin hankalin da suke ciki sbd yunwa da ciwo me karfin gaske na kokarin shigar babyn wadda tafara qanqamcewa ga Abdul din da shima wahala take neman kashesa da qananun shekaru. Abdul kuwa da ummansa sun koma masu baran karfi da yaji sbd duk zai tafi gurin aikin wahalar dayake yi binsa takeyi bata zama fitowa takeyi dan haka tare suke zuwa ya zaunar da ita guri daya wasu su bata sadaka sbd tinanin almajirace wasu kuma gudunta ma sukeyi. A cikin wannan halin sukai sati kusan uku sedai zuwa lokacin duk jamaar kauyen sun fahimci fatiman ta samu tabin kwakwalwa dan haka sadakar ma aka dena bata. ****FATIMA UMMITA shine sunan da Abdul ya sakawa qanwarsa dayake jinta kamar ransa dan kuwa shine me goyata da kansa duk yawon da zaiyi da ummansu yarinyar tana bayansa harya saba yanzu kauyukan gabansu suke zuwa tallan yalo dayake sara yana siyarwa. UMMITA daga baya umman na bata nono dan haka tafara lafiya ta koma cikakkiyar lafiyayyar baby sedai har lokacin sitirar sakawanta daya ce tak wadda mama sakina ta saka mata, Wanka kuwa sai suyi sati baayi mata ba sai daga baya yake kaita mama sakinata tayi mata harda hudan kunne tai mata ta saka ma yan kunne harda wasu kayan ta sake siya mata guda daya dan itama batada wani karfi. ##MAMUH #LIMBAS #ZAADENS #BESTSTORY #UMMITA LIMBA #JANNAH ZADEEN #DONOR ZAFAFA BIYAR KALBIM 500 mamuhgee A DUNIYATA 500 Huguma AJIYA A DUHU 500 Billyn Abdul KIRJIN ME HANKALI 500 Miss xoxo Pay at 0022419171 AccessBank Maryam sani gummi Shedan biya 09033181070 Or mtn vtu at 09032345899 *_Arewabooks@Mamuhgee_* 6 *ZUZEAMVENTURES* 08144015291 Aslm barkanmu da wannan lokaci Ina Mai farin cikin sanar daku cewa Zuzeam ventures takawo maku ingantattun magunguna masu inganci cikin Aminci Muna da kaya kamar haka Mallaka Maganin sanyi Maganin cire tumbiMaganin farin jini Maganin matsiMaganin mata Maganin sa ni’ima da dandano Dulka Amare Set na gyran jiki Set na amarya Tabaje tsumin Gomba Xuma kiba ta hips and Brest Magungunan gyran Brest Magungunan Karin hips Maganin sliming Muna da kaya masu inganci cikin sauki da rahusa Ina wadda keneman mallaka sahihiya quaranty wlh hajiya kixo ga zuzeam ventures xakiji ddin mallaka duk fadin ran ogah duk fadansa wlh sai yyi sanyi 08144015291 Idan maganin mata kikeso akwai Idan gyran jiki kikeso gyran fata gyran Brest magungunan sa kiba da hips DOMIN samunta Kai tsaye kira wannan no 08144015291 DOMIN mgn da ita whatapp 08144015291muna tura kayanmu ko ina cikin iKon allah 🥰👌🏻 Bononza Bononza Tsimin mangoro 1k🥭 Tsimin dabino 1k Gumba ukku balai 700 Gumba aya da nonon rakumi 700 Garin kafi ciccibi 500 Garin bata gaban kishiya 500 Matsin mallaka tada zaune tsaye 2500 Turaren mallaka ba aba mai kishiya 2500 Total kayan 9500 Za a bakisu akan 3800 Kuma mutun goman farko nadakyautar Abun 2k 🗣️🗣️🗣️🗣️🗣️🗣️ ASSALAMU ALAIKUM ALHAMDULILLAH YAN UWA NEW PROMO YA KAMMALA💃🏽💃🏽💃🏽😁😁😁 da 5k dinki ki kwashi kayan 12k hajiyata 💃🏽💃🏽💃🏽😃🙃Kazar gadali ta mallara Rabi 3500 Tsimin gam gam 1500 Ruwan kara zunzurutun dadı😋800 Garin 7in1 1k Gumba 3 balai 500 Gumba kwakwa da dabino 500 Infection ruwan tsarki 1k Garin zunzurutun dadi 1200 Matsin ba a fira d wando 500 Matsin infection mai matse mace gam 500 12k All at 5k kedai dannan link dinnan don samun naki ki maza kiyi bucking koda kudinki saida Rabonki ************ Malam AYOUB LIMBA ma'aikacin wata maaikatar qera robobi ne dayakeda gaskia da amana tareda kwarjini da farin jini sosai ga duk wanda yayi hulda dashi sbd gaskiyansa da hakurinsa tareda sanyin halinsa. Ayoub baida uwa a cikin matan babansa ya taso sbd tasa uwar ta rasu tin yana qarami, Cikin azabar yan ubanci data matar mahaifinsa ya taso babu sauki ko sassauci a halinda ya taso cikinsa a gidan mahaifinsa gashi mahaifin nasu bame zama bane yawon nema yake zuwa, Azaba da ukubar gidan ya sakasa zamowa me zafin nema da kokarin aiki wanda ya saka ya fara banbanta da yaran gidan sbd yanada 'da'a kokarin bin na gaba, A cikin masu aikin me gari ya samu ya shiga suna zuwa kauyuka cin kasuwa suna siyar masa da hatsi da albarkatun gona sukan yi kwana biyu basu dawo ba. Tin ana ganinsa yaro shekarunsa basu kai ba har kokarinsa ya kwacesa ya zama sharp yana iya huldodi sosai wanda ya saka ya samu matsayi me tsafta a zuciyar me gari daga nan ya hadasa da wasu mutanensa dake wani kauye masu zuwa birni suka fara zuwa dashi, Cikin kankanin lokaci acan ma ya samu mutane masu kaunarsa ya bar kauyen kwata kwata sedai yazo ganin gida Allah ya fara rufa masa asiri. A wannan lokacin da Megari yake tamkar mahaifinsa sbd kauna da kuma juya masa dukiyar dayake yi a can birin sbd shekarunsa sunja sosai ya zama matashi me gaskia da amana kwatsam Allah ya karbi ran maigari wanda hakan ya saka kaf yan kauyen masu hassadarsa suka taso suka zuga iyalan megarin suka kwace komai nasu tas basu bar masa komai ba. A cikin gidansu kaf daga yan uwansa har matan babansa harma maqota hassadarsa sukeyi dama matasan kauyen kaf sbd babu wanda ya taba fita birni nema a tarihin kauyen sai shi ya shiga cikin masu arziki harma da dan karatunsa ya koyo dan haka tsanarsa suke ji sosai da baqin cikinsa sbd babu me abinyi a cikinsu Gashi ko gona babansu baida bare suyi noma daga me saida rake sai me saida itace da dadai sauran irinsu da baa wani samun komai. Rasuwar me gari da wata hudu nasu mahaifin ya rasu dan abinda ya bari wanda duka idan aka hada bazaa samu dubu dari ba aka tattara aka raba aka bawa kowa ya tattara yabar kauyen. Watansa biyar da tafiya ya samu aiki a wani kamfanin qera roba wanda gurin qerawan yake wajen birni sosai harya zo kusa da kauyensu sosai dan haka sai hakan yai masa dadi dan babu jimawa ya fara gini a kauyen da dan qaramin filin daya siya. Aikinsa yana rufa masa asiri sosai dan abinda yake samu din yanayi ba laifi hakama shi kadaine dan kauyen a cikin kaf ma'aikatan gurin dan haka shine kusa yakeda sani sosai a bangaren dan haka kowa ya tashi neman abu shi ake nema. Hakurinsa da kwantar da kansa tareda rashin rawar kai ya saka yayi farin jini sosai da suna a gurin, Sabuwar hassada ce da baqin ciki ta sako yan kauyen da yan uwansa gaba daya suka fara kokarin ganin sun masa baqin ciki amma bai taba damuwa kuma yana taimaka musu sosai. A maaikatar yake kwana amma yana gama gininsa na qasa ya dawo gidansa daga nan yake zuwa aikinsa kullum akan kekensa sabuwa dal daya siya. Gama gidansa da wata uku ya hadu da Fatima da sakina qawayen da suka taso tare tin yarinta baa kauyensu suke ba kauyen kusa dasu, Fatima a hannun kawunta take sbd itama marainiya ce dan haka kawun na ganin Ayoub nada abin lasawa tini ya basa aurenta ba bata lokaci akai auren bayan tabarma da buta sai setin kayan cin abinci na silver babu abinda ya siya mata ya tattara aka kaita sedai daga baya ayoub ya siya musu katuwar katifa da abubuwan buqatarsu suka gyara gidansu. Zuwan sakina gurin fatima kauyen Allah ya hadata da baba ila shima ya aurota suka dawo zama kauye daya. Baba ila kwata kwata baya kaunar Ayoub dan yana cikin yan hassadarsa dan haka ya fara shiga tsakanin Amintar Sakina da fatima duk da sam sakina bata yadda da hakan ba saida fatima taga hakan zai fara kawo matsala a auren sakinar se ta dan ringa janyewa sbd a zauna lafiya. Shekara daya da auren cif Fatima ta haifi Namiji wanda Ayoub ya sakawa sunan Maigari wato ABDULAZIZ AYOUB LIMBA. Abdul ya taso mahaifinsa da ummansa suna tsananin sonsa da kaunarsa cikeda gata da kulawa musamman da mahaifinsa ya kasance masu dan karfi a kauyen, Ayoub baya barin Abdul fita waje wasa ko yawo kaman yanda yaran kauye sukeyi hakama sitiran sakawansa da cimarsu ma daban take me tsafta da wadata, Ayoub ya killace iyalinsa sam baya barinsu shiga mutane sosai sbd yasan baa kaunarsu a kauyen dan haka zaa iya cutatar dasu dan haka ko fatima bada kowa take hulda ba bayan danginsa wainda itama suka tsaneta da 'danta amma duk da hakan tana dan mu'amalantarsu. Abdul yana kaiwa shekarun fara karatu Ayoub ya sakasa primary school dake can local government kullum yana kaisa da keke ya daukosa idan antashi. Fara karatun Abdul ya sake banbantasa da yaran kauyen gashi ya taso baa wani shiga mutane dashi sai ya kasance baida iya muaamala da mutane, Gurin aikin babansa ne kadai yake sakewa yayi wasa sbd acan suna sonsa kasancewansa fari sosai Kyakkyawa sbd daga babansa har ummansa farare ne tas. Abdul ya dauko farin jinin babansa da kwarjini tin yana yaro duk inda akaje dashi idan ba kauyensu ba da bazasu taba sonsu ba sansa akeyi sosai. Abdul nada shekara goma sha uku ya zama wani irin nitsatsen yaro mai daukan ido da nutsuwan data kere ta masu shekarunsa wanda asalin miskilanci ne daya taso a cikinsa na tasowa kai daya ba abokin wasa sai iyayensa yai masa yawa gashi lokacin ilimin boko da addini duk babansa ya tsaya akai yana basa. A ranar wani jumaa da ayoub yayi kwana biyu yana kwana gurin aiki sesai ya dawo gida ya koma sbd ayyukan da sukai yawa gashi maaikatansu da yawa basa nan sbd lokacin baa gama dawowa hutun sallah bane. Ranar a gida ya wuni tareda Abdul sukaje local government sallan jumaa sukayo siyayyar kayan kwalama suka dawo Duk inda suka wuce take zakasan uba da 'da ne sbd kamanninsu dasuke bayyane. Suna dawowa gida a tsakar gidan fatima tai musu shimfida suka zauna dukkaninsu tana gyara musu su lemun da suka siyo da karas da harma da yalo suna fira suna ci. Ayoub bai bar gidan ba sai da yayi sallan ishai yai musu seda safe ya fice Abdul nai masa saida safe kaman ya bisa amma fatima ta hanasa duk da washe gari ba makarantar boko. Karfe biyun dare kauyukan kusa suka dauki hayaniyar gobara data tashi a ma'aikatar robobin take jamaa suka ringa fitowa cikik mamaki da tsoron kada wutar ta biyo daji tayo musu nan. Wasu kuwa haka kawai suka ringa godewa Allah da wutar sbd dukkanin baqin cikinsu akan maaikatar yake. Fatima dayake basa shiga huldodin mutane taji hayaniyar sama sama amma bata fito ba duk da ba baccin takeji ba kirjinta kawai takejin yayi mata wani irin nauyin gaske kamar numfashinta zai dauke, Ga Abdul a gabanta sai wani irin gumi yakeyi kamar yana mafarki mara dadi. Hannunta da yai mata nauyi ta miqa inda yake kwance kan katifarsa ta tayar dashi tana karanta masa addua. Bude idanuwansa yayi tareda tashi zaune. Ajiyar zuciya ya ringa jerowa yana hada zufa tana share masa kafin tace "Tashi je ka wanko fuskarka kayo alwala kazo kayi sallah kayi mana addua ni banajin dadi." Miqewa yai ya nufi kofa ya fito tsakar gidan wanda yana fitowa abind kunnuwansa suka fara ji shine ihun da mutane keyi suna cewa "GOBARA TA KONA GIDAN ROBAR SU AYOUBA" kalmar da harya mutu bazata taba fita daga kansa da kunnuwansa ba. Faduwa gabansa yai tsoro me tsananin gaske ya shigesa ya juyo da sauri zai kalla ummansa ashe itama ta jiyo hakan. Tana fitowa tsakar gidan ko takarmi bata tsaya sakawa ba ta nufi kofar fita gidan tana saka hijabin dayake hannunta. Bayanta Abdul din yabi jikinsa na rawa tsoro na shigarsa. Tafiya takeyi kamar mahaikaciya Abdul na riqe da hijabinta batareda sunsan insa suke jefa kafafunsu ba. Fitarsu gidan ashe ana ankare dasu suna yin nisa aka fada gidan aka kwashe musu kusan fiyeda rabin kayansu da abubuwansu harda katuwar katifarsu. Tafiya me dan tsayi sikai tin daga nesa taji ana fadar wanda suke ciki mutum uku ne sedai ayi hakuri dasu dan kam babu ta yanda zaa iya fiddasu. Sarewa kafafunta sikai ta kife a gurin Abdul yayi saurin kamota jikinsa na rawa yana kiran sunanta. Da rarrafe ta qaraso Abdul din na kamata duk da tafi karfinsa. Da sauri aka riqeta tana kokarin yi cikin wutar tana kiran Ayoub da karfi jikinta na wani irin rawa da tashin hankalin dayake neman juyar mata da kwakwalwa. Abdul ma kuka yakeyi sosai yana kiran sunan babansa shima yana kokarin tafiya ana riqesa yana ihu me karfin gaske. #MAMUH #LIMBAS #BESTYSTORY #BESTLOVE ZAFAFA BIYAR KALBIM 500 mamuhgee A DUNIYATA 500 Huguma AJIYA A DUHU 500 Billyn Abdul KIRJIN ME HANKALI 500 Miss xoxo Pay at 0022419171 AccessBank Maryam sani gummi Shedan biya 09033181070 Or mtn vtu at 09032345899*_Arewabooks@Mamuhgee_* 7 *ZUZEAM VENTURES* Best APHRODISIAC 08144015291 Aslm barkanmu da wannan lokaci Ina Mai farin cikin sanar daku cewa Zuzeam ventures takawo maku ingantattun magunguna masu inganci cikin Aminci Muna da kaya kamar haka Mallaka Maganin sanyi Maganin cire tumbiMaganin farin jini Maganin matsiMaganin mata Maganin sa ni’ima da dandano Dulka Amare Set na gyran jiki Set na amarya Tabaje tsumin Gomba Xuma kiba ta hips and Brest Magungunan gyran Brest Magungunan Karin hips Maganin sliming Muna da kaya masu inganci cikin sauki da rahusa Ina wadda keneman mallaka sahihiya quaranty wlh hajiya kixo ga zuzeam ventures xakiji ddin mallaka duk fadin ran ogah duk fadansa wlh sai yyi sanyi 08144015291 Idan maganin mata kikeso akwai Idan gyran jiki kikeso gyran fata gyran Brest magungunan sa kiba da hips DOMIN samunta Kai tsaye kira wannan no 08144015291 DOMIN mgn da ita whatapp 08144015291muna tura kayanmu ko ina cikin iKon allah 🥰👌🏻 Bononza Bononza Tsimin mangoro 1k🥭 Tsimin dabino 1k Gumba ukku balai 700 Gumba aya da nonon rakumi 700 Garin kafi ciccibi 500 Garin bata gaban kishiya 500 Matsin mallaka tada zaune tsaye 2500 Turaren mallaka ba aba mai kishiya 2500 Total kayan 9500 Za a bakisu akan 3800 Kuma mutun goman farko nadakyautar Abun 2k 🗣️🗣️🗣️🗣️🗣️🗣️ ASSALAMU ALAIKUM ALHAMDULILLAH YAN UWA NEW PROMO YA KAMMALA💃🏽💃🏽💃🏽😁😁😁 da 5k dinki ki kwashi kayan 12k hajiyata 💃🏽💃🏽💃🏽😃🙃Kazar gadali ta mallara Rabi 3500 Tsimin gam gam 1500 Ruwan kara zunzurutun dadı😋800 Garin 7in1 1k Gumba 3 balai 500 Gumba kwakwa da dabino 500 Infection ruwan tsarki 1k Garin zunzurutun dadi 1200 Matsin ba a fira d wando 500 Matsin infection mai matse mace gam 500 12k All at 5k kedai dannan link dinnan don samun naki ki maza kiyi bucking koda kudinki saida Rabonki ************ Gawar da aka jera part part dinta kamar gawayi a gabansu ne ya saka ummansa somewa a gurin shima zubewa yayi a gurin yana wani irin jijjigar data saka daya daga cikin abokan aikin baban nasa dake gurin rungumesa ya qanqamesa da karfi yana kira masa sunayen Allah tareda addua. Umma kuwa maza ne suka zuba mata ruwa a gurin sbd babu mata a gurin dan girman lamarin itama dan tanada dolenta ne a cikin wutar ta iso gurin batareda ta sani ba. Tana farfadowa ta sake somewa jini na balle mata a gurin wanda babu wanda ya lura sbd duhu da kuka tashin hankali duk da anriga anyi asuba a lokacin. Abdul dinne ne da aketa tofawa addua ya lura da umman tasa da gudu yayi kanta yana kallan jinin daya bata kayanta. Daidai nan sakina ta iso gurin cikin matsanancin tashin hankalin daya sake daga hankalin Abdul da tsoro sbd kwasar umman da akai zuwa gida hankali tashe. Suna isa gida mama sakina cikin gaggawa ta taimakawa fatiman jinin ya tsaya ta kwantar da ita tana karanta mata yan adduain data sani tinda ba wani ilimi me zurfi ne dasu sosai ba. Rasuwar Ayouba tayiwa fatimar mummunan dukan daya saka cikin da basusan dashiba kusan zubewa, Ayoub ne gatanta, Ayoub ne a matsayin uwa da ubanta da danginta sbd batada kowa bayan kawunta wanda ya aurar da ita ya tattarata ya watsar sbd daman neman hanyar rabuwa yake da ita ya huta daga wahalar dayake ganin yanayi da ita. Ayoub baida uwa baida uba sai yan uba da matan mahaifi wanda sukafi son balai akansa, Waye zai zama gatanta dana yayanta a duniyar yanxu? Abdul yayi kuka yayi kuka harya rasa ya zaiyi wani kukan sbd gawar mahaifinsa da aka jera masa baisan yaya zaiyi da ita ba, Durkusawa yayi gaban gawar yana sake fasa wani sabon kuka kirjinsa na wani irin radadin da baisan mene ba. Baba Ahmed wanda yake abokin aikin baban shine ya karbi ragamar komai sbd karfe tara na safe ma ta kusa kusan dukkanin maaikatansu na nesa da kusa sun iso tardda yan kallo na kauyen da makotan kauyen dan haka ba bata lokaci akai taho gida aka hada gawar aka yayyafa mata ruwan wankan gawa sbd bazaa iya maza wankan ba aka hadasa a farin likafaninsa aka nade akai masa janazah a kofar gidansa inda ya samu mutane daidai gwargwado sbd a cike kauyen yake ranar da mutane sbd abinda ya faru. Tinda Abdul ya rungumi gawar babansa dayake nade a kyalle yaji zuciyarsa na wani irin ciwo da nauyi kaman zata zazzago tareda wani irin radadi kaman tana bushewa. Kukansa daukewa yayi tsaf saida aka dawo daga kai baban ya dawo gida shi kadai batareda wani ya biyosa ba yana shigow gidansu ya tararda ummansa kwance daga ita sai mama sakina da wasu daidaikun mutane da suka gama gaisuwa suka miqe suka fice. Tahowa yayi ya zauna gefen ummansa wadda ta dago jajayen idanuwanta da sukai mata tsananin nauyi ta xuba masa shima ita ya kalla ya sunkuyar da kansa wasu hawaye masu tsananin zafi suka gangaro masa suna sauka qasa gabansa. Mama sakina ma kasa riqe kukanta tayi tafara hawaye masu zafi tana rufe fuskanta da tafukan hannayenta. Duka a cikinsu babu wanda ya damu koma tsayawa tantance irin satar da akai musu a gidan bayan fitarsu mama sakina ma data lura batai magana ba sbd radadi da ake cikinsa. Shiru gidan yayi har yamma babu wanda ya sake shigowa gidan sedai ayi sallama abdul din ya fita idan abokan aikin baban sukazo amma ko yan gidansu Ayoub din tinda safe suka zo akai komai dasu daga nan suka watse kowa yake harkan gabansa. Mama sakina tayi abinci tayi duk dubaran da zatai suci babu wanda ya iya cin komai a tsakaninsu dan haka ta hakura itama bata iya cin abincin ba sbd har cikin rai da jininta take jin ciwo da radadin da fatima ke ciki sbd kaunar datake tsakaninsu me girman gaske ce wadda suka taso a cikinta tin yarinta sbd itace ta zama kamar gatan fatima tin suna qananu har girmansu sbd ita tanada mahaifiya sabanin fatima data taso ba uwa ba uba. A gidan mama sakina ta kwana duk aike da fadan da baba ila yai mata bata koma ba dan haka ya zuba mata ido yaga gudun ruwanta. Washe gari da safe shugaban gurin aikinsu Ayoub din ya taho gaisuwa ya kawo musu abinci sosai da abubuwan buqatarsu tareda biyan kudin makarantar Abdul din wadda yake a local government harya gama. Yaso bada kudin dayake ganin kaman diyya ce zai biya amma ganin Abdul din yaro ne kuma matar ayoub din batada me tsaya mata hakama yan uwansa sun saka zalamar jiran ya bayar sai kawai ya fasa ya fadawa baba Ahmed idan Abdul din yagama karatu ya isa fara business zai basa da hannunsa insha Allah kuma zai rubuta hakan ya ajiye koya mutu bashi ne Abdul yake binsa zaa basa. Babu wanda yasan da hakan sai baba Ahmed wanda yayi naam da hakan dan haka bayan tafiyar alhaji Kabir din shima Ahmed tafiyarsa yayi sbd ba maganar aiki a gurin yanxu sbd kamfanin dai ya mutu mutus sai ansake sabon ginin ma dan haka yanzu maaikatan duk sun tafiyarsu sai kuma an sake ginin kamfanin akan wannan tukuna. Kwanan mama sakina bakwai a gidan yan kauyensu suka taho gaisuwa da matan kawun fatiman dashi kansa da wasu yan uwan sakinar da yawansu. Fatima a cikin kwanakin ta zama abar tausayi sbd abinci ma bata iya ci haka kawai cikin jikinta ya hanata lfy sbd damuwa da tsananin quncin da zuciyarta take ciki. Abdul ganin halinda mahaifiyarsa take ciki shima ya tabasa dan haka kwata kwata baya cikin walwala ko kadan daman babansa shine abokinsa kuma abokin wasansa sbd baya fita koina wasa bai sababa tin tasosawarsa. Mama sakina ma bata cikin walwalan kwata kwata sbd ganin halinda suke ciki dan haka bayan yan garinsu sun koma itama ta koma gida sedai duk bayan kwana daya sai tazo ta dubasu. Kawun fatiman da zai tafi ganinsu da abinci sosai baiji tausayi ko kunya ba ya diba abincin sosai ta tafiyarsa. Yan uwan ayoub din ma da sukaga hakan suma suka taho suka debi abincin me yawa sosai da cewa ai suma sunada gadon Ayoub dan haka tinda baibai komaiba a basu abincin. Abdul ne rayuwarsa tafara sauyawa sbd karatunsa daya fara rawa sbd kulawa da mahifiyarsa wadda ta kasa dangana da rashin baban dan haka lafiya kwata kwata tafara kaurace mata, Ta rame ta koma kamar wadda bata taba lafiyaba rayuwarta, Bata wani ci bata wani sha bata cewa komai sai dole ga cikinta yanata girma dan haka komai a gidan shine yakeyi masu, Shine yake musu wanki,ya dafa musu abinci,ya kai mata ruwan wanka yayi shara ya nemo,ya kuma tafi makaranta,sannan ya zauna yasha kuka a duk lokacinda ta kasa riqe abinda takeji tafara kuka haka yake yi a tareda ita,idan ciwo ya taso mata ma shine me zaunawa ya kula da ita ba magana haka zatai ta warke sbd basuda komai. Ahankali baba ila ya gaji ya hana sakina zuwa gidan kaman yanda ta saba dan haka duk abinda suke buqata sedai Abdul din yake ya karbo musu dan abincin da zasu ci da wasu abubuwan kaman sabulun wanka ko omon wanki. Hakan ma baba ila ganin yayi kaman zaa karya tattalin arzikin gidansa duk da na sakinar ne take basu dan haka ya haukace musu yace ya hana, Ahankali rayuwa tafara yi musu tsananin gaske sbd komai basuda shi basuda me basu basuda hanyar samu, Umma ta koma masa kamar me tabin hankali yau lafiya gobe ciwo kwata kwata batada sauran lafiyar ma da zata san tawakkali da dangana bare tasan itace ya kamata ta dauki juriya ta kula da Abdul ta tsaya masa sedai shine ya koma ya tsaya akanta. Tsana me tsananin gaske Baba ila da yan gidansu Ayoub sukai masa sbd yanda tin yan yaro ya tsayu kan uwarsa gashi yai neman taimakon a gurinsu amma sun bayyanar masa da tsanar da sukaiwa mahaifinsa a fili dan haka sai yaji yafisu jin tsanarsu me tsananin gaske dan haka bai sake ko bi ta hanyar kofar gidansu ba Dan yafison mutuwa ta daukesa kaman yanda ta dauko babansa daya sake zuwa gurinsu. Baba ila kuwa sbd tsananin kaunar datake tsakaninsu da mama sakina dayake jinta kaman ummansa data haifesa yasa yake danne ciwo da radadin tsanar da yayi musu sbd mama sakina ta tabbatar masa har abada kada yace zai rabu da ita sbd itama uwarsa ce ko fatima na raye ko bata raye. Rayuwa tafara yiwa mama sakina tsanani itama sbd baba ila daya dena bata komai sbd kada ta taimaka musu daman matansa da yayansa kwata kwata basa kaunarta, Abincin da zata ci kansa ankoma a gidan a qaramar roba ake bata shi wanda ita kanta baya isarta amma a hakan wata ran take juyewa a leda ta bawa Abdul din ya kaiwa fatima wadda da kansa yake bata itama bata wani ci kadan take ci sbd yanayinta. A haka ya dage yana karatunsa duk da wata rana yaje ne wata ran baya zuwa amma a hakan yana kokari sosai Suma malamansa da suka gaji da dukansa aka fahimci tsananin rayuwar dayake ciki sai aka dena dukansa aka barsa a hakan idan yazo shikenan idan baizo ba shikenan. Mama sakina ta koma sabulun da zatai wankan ita kanta batada shi batada ko man shafawa masifar rayuwa tafara sakota gaba dan haka Abdul din daya fahimci hakan saiya rage zuwa kwata kwata gurinta yafara aikin wahala da wanda zai iya da wanda bazai iyaba haryafara sabawa idan ya samo yana dan siya musu harma da ita mama sakinan yana bata omo ko wani abin idan ya siya musu. Sun wayo gari sitirar sakawa tai musu wuya daga shi har ummansa sbd sata da aka ringa sakasu gaba da ita saida suka rasa komai a gidan bayan tabarma data mutu sai karamar katifar da itama ta mutu sai kuwa buta daya da bokitin wanka da tukunya shi kadai suka rage musu. Cikin ummansa ya tsufa harya wuce lokacin haihuwa a lokacin ne katangar gidan ruwa ya zubar musu da ita aka sace duk kwanon langa langar gidan da sauran abubuwan dan haka suke a rabe a gefe cikin gidan wanda har dakin da suke ruwa yake daga saman sbd har saman anhau an sace langalanga kadan aka bar musu dan haka idan ana ruwa suna gefe dan ruwan yana dan shigowa kadan kadan ta sama. #MAMUH #BESTLOVE #BESTROMANCE #HOT #STRUGGLE #BILLIONAIRES WAR #AY LIMBA ZAFAFA BIYAR KALBIM 500 mamuhgee A DUNIYATA 500 Huguma AJIYA A DUHU 500 Billyn Abdul KIRJIN ME HANKALI 500 Miss xoxo Pay at 0022419171 AccessBank Maryam sani gummi Shedan biya 09033181070 Or mtn vtu at 09032345899*_Arewabooks@Mamuhgee_* 8 *ZUZEAM VENTURES* Best APHRODISIAC 08144015291 Aslm barkanmu da wannan lokaci Ina Mai farin cikin sanar daku cewa Zuzeam ventures takawo maku ingantattun magunguna masu inganci cikin Aminci Muna da kaya kamar haka Mallaka Maganin sanyi Maganin cire tumbiMaganin farin jini Maganin matsiMaganin mata Maganin sa ni’ima da dandano Dulka Amare Set na gyran jiki Set na amarya Tabaje tsumin Gomba Xuma kiba ta hips and Brest Magungunan gyran Brest Magungunan Karin hips Maganin sliming Muna da kaya masu inganci cikin sauki da rahusa Ina wadda keneman mallaka sahihiya quaranty wlh hajiya kixo ga zuzeam ventures xakiji ddin mallaka duk fadin ran ogah duk fadansa wlh sai yyi sanyi 08144015291 Idan maganin mata kikeso akwai Idan gyran jiki kikeso gyran fata gyran Brest magungunan sa kiba da hips DOMIN samunta Kai tsaye kira wannan no 08144015291 DOMIN mgn da ita whatapp 08144015291muna tura kayanmu ko ina cikin iKon allah 🥰👌🏻 Bononza Bononza Tsimin mangoro 1k🥭 Tsimin dabino 1k Gumba ukku balai 700 Gumba aya da nonon rakumi 700 Garin kafi ciccibi 500 Garin bata gaban kishiya 500 Matsin mallaka tada zaune tsaye 2500 Turaren mallaka ba aba mai kishiya 2500 Total kayan 9500 Za a bakisu akan 3800 Kuma mutun goman farko nadakyautar Abun 2k 🗣️🗣️🗣️🗣️🗣️🗣️ ASSALAMU ALAIKUM ALHAMDULILLAH YAN UWA NEW PROMO YA KAMMALA💃🏽💃🏽💃🏽😁😁😁 da 5k dinki ki kwashi kayan 12k hajiyata 💃🏽💃🏽💃🏽😃🙃Kazar gadali ta mallara Rabi 3500 Tsimin gam gam 1500 Ruwan kara zunzurutun dadı😋800 Garin 7in1 1k Gumba 3 balai 500 Gumba kwakwa da dabino 500 Infection ruwan tsarki 1k Garin zunzurutun dadi 1200 Matsin ba a fira d wando 500 Matsin infection mai matse mace gam 500 12k All at 5k kedai dannan link dinnan don samun naki ki maza kiyi bucking koda kudinki saida Rabonki ************* Koda cikin Fatima ya isa haihuwa karfin da zatai naqudar arziki batada shi sbd yunwa da ciwo tareda cikin da duk ya janyeta ta koma kana ganin qashin bayanta ya fito dosai da duk qashin kirjinta kana ganinsu idanuwanta sunyi ciki sosai tayani muni dik ya gama sauya kamanninta sbd ciwon da yunwar da bayan Allah da yayita babu abincin da zai dawo da ita yanda take kila. Abdul yana kokarin daya fi na shekarunsa sbd har local government yake zuwa nema da aiki harma da tallan rage wadda bayayi da yawa sbd baya iya dadewa waje yake komawa gida gurin ummansa dan komai shine yake mata sbd baba ila ya rabasu da Mama sakina wadda take cikin tsananin daci da ciwon rai na hakan amma Abdul dinne ya roketa akan kada ta rabu da baba ila sbd su shiyasa kawai take zaune a gidan amma aurensa gabaki daya ya fita daga zuciyarta ba sauran sonsa ko qwaya daya a ranta gashi daman Allah bai bata haihuwaba tayi neman haihuwar harta gaji ta barwa Allah. A cikin wannan halin da suke ciki ne Allah ya kawowa Umman naquda cikin ciwo da ukubar rayuwa tareda yunwar data gama kame duk wani kayan cikinta da gangar jikinta ta haihu, Haihuwar data taho musu da sabuwar kaddarar da babu yanda zasuyi bayan rungumar rayuwa a yanda taxo musu batareda taimkon kowa ko kulawan kowaba bayan ta mama sakina da suke samu jefi jefi Abdul ya reni kanwarsa da mahifiyarsa wadda ta koma masa tamkar UMMITA wadda take yar shekara biyu zuwa uku dan kuwa duk inda zashi dasu yake zuwa sbd fita sukeyi su tafi yawo dan haka duk inda zashi yanzu suna tare dan haka da yawa ake musu kallan almjirai ko yan yawon neman sadaka duk da yana iya kokarinsa akansu gurin ganin ya tsaftace su. Yanzu sun dena zuwa irin guraren dake kaman kasuwa ko tasha gurin aikin nema ko sanaa sbd bayason ana kallan ummansa da ummitan dan haka Local government yake zuwa dasu har makarantarsa wadda yake gaf da kammalawa yanzu. Har ciki a ke barinsa shiga dasu saiya kaisu bayan ajinsu yace su zauna karsu tashi saiya gama ya fito. Haka zasu sauna suyita wasa a gurin harya gama batareda da damuwa da abinda dalibai ke fada akan mahaifiyarsa da rabin ransa dayake jinta kaman shine babanta sbd BAABAH take kiransa dan bata san kowa ba bayanshi da ummanta hakama shi take kallo ubanta tinda umman ta koma kaman ita tare suke wasa duk da umman ta dena magana. Daga makaranta shagon dayake aiki yake wucewa dasu ya siya musu abinci suci ya ajesu guri daya suyita walwalansu harya gama se yamma su nufo gida sbd baya kaiwa dare sbd su duk da megidansa yana son ya ringa kwana shagon sbd yadda dashi da yayi da kuma kokarinsa tareda amanarsa amma sam baya iya hakan sbd kare mutuncin ummansa da Ummitansa dan haka duk abinda yake samu a aiki ko sanaa yamma nayi yake wutowa gida dasu su wanka suci dan abinda ya samu ya ringa koyawa ummita dan karatun yara har suyi bacci itada umman ya gyara musu gurin kwanciya ya kaisu su kwanta shima ya zauna gadinsu dan baccinsa rabi da rabi ne akansu sam bayada wata irin yadda da kowa gashi basada koda rabin gidan a zube dan haka baya wani bacci akansu. Ranar wata alhamis ya samu wani aiki a wani sabon kamfani da zaa gina a local government na gyaran shinkafa me kudin dayafi tsaron shagon dan haka ya karba ya hada biyu yana yi sedai aikin gurin akwai hadari dan haka dole yake barin su ummita a gida amma saiya fada musu yafi so ashirin kada su fita koina. Sunji maganarsa basa fita dik ya tafi harya dawo baya cikin nutsuwa amma yana tarar dasu a gida basa fita koina sedai gidan zai tarar anyi masa kaca kaca hakama sunyi wata irin dauda hakanan zai tsaftacesu ya gyara gidan ya basu abinci suci su koshi suyi sallah wadda tasa ce kawai ta arziki su kam ture ture sukeyi a gurin sallan tsakanin umman da ummita yana jinsu zai kyalesu a gama a hakan. Akwai wata irin kauna da so me tsananin gaske tareda shaquwar datake basa tsoron da baisan na mene ba a tsakaninsa da Ummansa da Ummitansa haka suke sakasa wasa dasu dole wanda su kadai ne suke ganin dariyarsa da walwalwansa dan Allah ya sako masa wani irin kame kai tin yana yaronsa shiyasa ya taso hakan. Tin yana fargaban barinsu a gida yaje ya dawo harya dan rage fargaban yana aikinsa cikin dan nutsuwa amma bawai hankalinsa baya gidan bane dan baya kara ko minti daya yana tashi aiki yake komawa gidan dan ya dena zuwa makaranta exam kawai yake jiran ranar yinta yazo ta gamawa tinda suka shiga ss3 ya dena zuwan waec kawai yake jiran yi. A yau tinda ya kamo hanyar zuwa gida yakejin baida nutsuwa dan haka ya qara sauri yana jin kirjinsa na nauyi ya kuma saba da hakan a duk lokacinda bay taredasu jin yake zuciyarsa ta ringa shiga damuwa da nauyi kenan. Yamma ne sosai dan haka bai biya gidan mama sakina ba dan bata sabulu da omon daya siyo harda ita ba dan haka ya wuce gida saiya dubosu saika ya fito dasu yaje ya kai mata batareda ya shiga gidan ba san anjima da baba ila yai masa iyaka da shigar masa gida sedai ya tsaya daga waje gefen gidan mama sakinar ta fito ko kawai ya aika mata ummita ta shiga takai ta fito shikuma yana waje yana jiranta su koma. Yana doso gidan tin bai karasa ba ya hango Ummita tana fitowa daga hanyar bayan gidansu tana kuka hannuwanta da kafafunta qasa da jini. Wani irin abu ne ya daki kirjinsa da tsakiyar kansa dan haka da sauri ya qaraso ya tarbeta tareda ajiye kayan hannunsa ya jawota gaba daya jikinta yana kallan hannuwanta muryansa dayake da wahalar ji shima dan baya wani magana sosai sbd baida abokin firar yace "Ina ummah? Meya faru? Kuka takeyi sosai ta juya bayanta ta nuna masa hanyar data fito tana cewa "Umma ta tafi, Dodo ya bita da gudu ta tafi...... Wani mummunan yawu me dacin gaske ya hadiye yana daukan ummitan ya nufi hanyar data nuna batareda ya tsaya fahimtar me take fadaba yana jin kaman kansa zai zare. Duhun magriba yayi amma sam baya ma gani ya doshi hanya yana tafiya yana duba umman kaman zai zai haukace a take yaji yana ji dan haka ummitan dake jikinsa ya sake qamqamewa yana jefa kafarsa duk inda ya samu yana adduar Allah kada ya jarabcesa da wannan jarabawar me girman gaske akan mahaifiyarsa da ita da ummita sune rayuwarsa da hasken dayake gani a wannan rayuwar ko yaya ummansa ta koma yana tsananin buqatanta a hakan. Tafiya yakeyi harya isa wani kauye duhu yai sosai amma kwata kwata baya hayyacinsa. Kaf kauyen babu ummansa babu wanda ya ganda dan haka ya juyo ya dawo kauyensu lokacin tini akai ishai amma be zauna ba ya zagaye kauyen tas nanma babu umman ga ummita wahala da zazzabin raunikan jikinta sun saka tayi bacci a jikinsa jikinta zafi sosai. Bai taba shiga mafi munin tashin hankali da firgici irin daren ba na rashin umman amma bai damu da daren ba haka ya doshi wani kauyen a cikin tsananin duhun dare nemanta idanuwansa sunyi wani irin mummunan jajir. A cikin dare mafi tashin hankali a rayuwarsa kauyuka uku ya zagaye amma kwata kwata babu ummansa babu wanda ya ganta dan haka ya yanke jiki ya fadi qanqame da ummita zazzabi me mugun karfi ya gama gabalaitar da ita a jikinsa. Jamaar kauyen daya somen suka yo kansa sbd lokacin har anfito sallan asuba gari ya waye sosai suka yo kansa suna son cire ummita a hannunsa amma yai mata wani irin mugun riqo da dole tana jikinsa aka zuba musu ruwa a tare. A tare suka sauke ajiyar zuciya sedai kowannensu a galabaice musamman ummita shi kuwa ganin yayi kaman baya ganin komai sbd azaba da wahala tareda galabaita da tsananin tashin hankali. Tashi zaune yayi yana gyarawa ummita zama a jikinsa yana sake rungumeta da kyau wasu zafafan hawayen daya manta rabonsa daya zubo suka gangaro daga fararen idanuwansa da suka koma jajir ya ambaci sunan umman ahankali yana rokon ALLAH ya kawo masa kowacce irin jarabawa indai ummansa zata dawo garesa zai jure ya runguma kaddarar. Tausayinsa ne ya rufe jamaar gurin dan haka aka taimaka masa aka tayasa bincika neman umman tasa a kauyen amma har yamma babu labarinta kuma har dayan kauyen suka tayasa nemanta amma babuta. Kauyensu ya nufo ummita na jikinsa a some sbd ruwan saman da akeyi sosai duk ya qare akansu. Koda ya dawo kauyensu ana sallan ishai duhu yayi sosai, Kofar gidan ya shiga wanda ruwan sama ya cika gidan kai tsaye dakinsu ya nufa ya bude ya shiga Taku daya yayi zuwa biyu kafafunsa suka kasa daukansa ya zube a gurin yana fasa wani irin kuka me karfin gaske Ummita dake jikinsa azaba ta farfado ta bude idanuwanta daqyar batada karfin motsawa anan ta sake lumshe idanuwanta suka rufe jikinta ya sake sakewa alaman ta sake fita hayyacinta. Kuka yakeyi sosai yana wani irin jijjiga zuciyarsa kaman zata fashe akan abinda yake ji, Shima zazzabine sosai me karfin gaske a jikinsa amma ya kasa sakin Ummita barema yasan shika halinda yake ciki. Kuka me yawa sa karfi sosai da idan da ba ruwa akeyib kusan duka makotan dake kusa sai sun jiyosa amma karfin ruwa bai bari anjisu ba. Ummansa yasan a duk inda take tana cikin wannan ruwan da duhun dare wanda zai firgitata ta qarasa haukacewa mutane su kyareta su qyamacet su hantareta shikenan ta shiga gagarin da babu wani gata ko rufin asiri gareta........ Wannan ke saka zuciyarsa daukan wani irin nauyi kaman zai haukace shima yakeji ya fasa kukan da babu me jinsa bayan Allah dayake fatan ya kawo masa dauki da sassauci a wannan rayuwar. Tsakar dare sosai ya dago jajayen idanuwansa da sukai nauyi da kumbura ya kalli ummita datake a sake jikinsa ya miqe ya koma gefen da babu sanyi a adakin ya gyara gurin kwanciyarsu ya kakkabe duk da baya ganin komai ya sauya mata kaya sbd na jikinta akwai sanyi ya kwamtar da ita. #MAMUH #BESTSTORY #BESTLOVE #BROTHERS LOVE #LIMBAS #ZADEENS ZAFAFA BIYAR KALBIM 500 mamuhgee A DUNIYATA 500 Huguma AJIYA A DUHU 500 Billyn Abdul KIRJIN ME HANKALI 500 Miss xoxo Pay at 0022419171 AccessBank Maryam sani gummi Shedan biya 09033181070 Or mtn vtu at 09032345899*_Arewabooks@Mamuhgee_* 9 *ZUZEAM VENTURES* Best APHRODISIAC 08144015291 Aslm barkanmu da wannan lokaci Ina Mai farin cikin sanar daku cewa Zuzeam ventures takawo maku ingantattun magunguna masu inganci cikin Aminci Muna da kaya kamar haka Mallaka Maganin sanyi Maganin cire tumbiMaganin farin jini Maganin matsiMaganin mata Maganin sa ni’ima da dandano Dulka Amare Set na gyran jiki Set na amarya Tabaje tsumin Gomba Xuma kiba ta hips and Brest Magungunan gyran Brest Magungunan Karin hips Maganin sliming Muna da kaya masu inganci cikin sauki da rahusa Ina wadda keneman mallaka sahihiya quaranty wlh hajiya kixo ga zuzeam ventures xakiji ddin mallaka duk fadin ran ogah duk fadansa wlh sai yyi sanyi 08144015291 Idan maganin mata kikeso akwai Idan gyran jiki kikeso gyran fata gyran Brest magungunan sa kiba da hips DOMIN samunta Kai tsaye kira wannan no 08144015291 DOMIN mgn da ita whatapp 08144015291muna tura kayanmu ko ina cikin iKon allah 🥰👌🏻 Bononza Bononza Tsimin mangoro 1k🥭 Tsimin dabino 1k Gumba ukku balai 700 Gumba aya da nonon rakumi 700 Garin kafi ciccibi 500 Garin bata gaban kishiya 500 Matsin mallaka tada zaune tsaye 2500 Turaren mallaka ba aba mai kishiya 2500 Total kayan 9500 Za a bakisu akan 3800 Kuma mutun goman farko nadakyautar Abun 2k 🗣️🗣️🗣️🗣️🗣️🗣️ ASSALAMU ALAIKUM ALHAMDULILLAH YAN UWA NEW PROMO YA KAMMALA💃🏽💃🏽💃🏽😁😁😁 da 5k dinki ki kwashi kayan 12k hajiyata 💃🏽💃🏽💃🏽😃🙃Kazar gadali ta mallara Rabi 3500 Tsimin gam gam 1500 Ruwan kara zunzurutun dadı😋800 Garin 7in1 1k Gumba 3 balai 500 Gumba kwakwa da dabino 500 Infection ruwan tsarki 1k Garin zunzurutun dadi 1200 Matsin ba a fira d wando 500 Matsin infection mai matse mace gam 500 12k All at 5k kedai dannan link dinnan don samun naki ki maza kiyi bucking koda kudinki saida Rabonki ******** Tashi yayi ya fito cikin duhun ya sauya kayansa yaje toilet ya fito yayi alwala ya dawo dakin A gefen ummita yayi sallah yafara sabon kuka yana fadawa Allah ummansa kadai yake fatan Allah yabata kyakkyan kariya tareda fatan dawowa garesa. Har akai asuba yana fadawa Allah ummansa tareda neman jariya da yadda da duk kaddarar da zata tinkarosa a rayuwa ya basa ikon inganta rayuwar Ummitah har mutuwarsa. A gida yayi sallar asuba bai fita ba kaman yanda yakeyi a baya, Yana gamawa ruwan zafi yai dubara ya dora yazo ya gasa ummita dasu sosai ya mayar mata da kayanta ya fita yaje ya samo mata koko da kosai ya dawo ya bata kaman ma dura mata yayi. Bai gama bata ba tayo masa amansa a jikinsa ya tashi yaje ya gyara mata jikinta ya sakeyi wanka shima ya sauya kaya ya sake bata kokon amma wannan karan batai masa amansa ba dan haka ya kwantar da ita tayi bacci har lokacin jikinta akwai zazzabi. Basuda wasu kayan dan haka ya wanke musu wainda duka lalace sbd kada su fita dana jikinsu su dawo babu wasu na sakawar dan haka yana gama shanyawa ya dauketa suka fice. Local government ya nufa acan yakaita wani chemist aka dubata akai mata allura aka basu magani ya siya mata bread sa freshYo na roba shikenan kudin hannunsa suka qare suka zagaya sosai nan ma ya bincika ummansa amma ba labari sai yamma sosai suka dawo gida. Kwantar da ita yayi ya gyare gidan fes kafin yayi sallan magrib suka shige dakinsu ya rufe. Yana yin sallan ishai kadan yaci bread din data rage da ruwa ya kwanta gefenta tareda rufesu sai a lokacin wani baccin azaba shima ya daukesa. Seda aka fito sallah ya farka yayi sallah yayita addua har gari ya waye sosai ya fito baida ko sisin siya mata abinci dan haka ruwan wanka kawai ya samar musu sukai wanka ya dauketa suka fice zuwa gurin aikinsa. Koda ya isa sbd rashin zuwansa kwana biyu tini aka saka wani a maimakonsa dan haka sedai ya tayasu suka dan hada masa dan abinda ya samu ya siyawa Ummitan Wainar gero taci yabata magani daganan ya nufi shagon dayake aiki a baya ko zai samu a karbesa suma. Yama xuwa shima ya riga ya samu wani amma dai yace ya tsaya ko miqa abu ne idan an siya ya taya wanda yake shagon yanzu a dan ringa basa wani abin. Haka ya zauna a bakin shagon da ummita wadda take lafe jikinsa har dare suka kai kafin ya basa 200 ya dawo gida. Suna dawowa tuwo ya siya mata da 200 din taci kadan tasha magani ya cinye sauran yasha ruwa yai sallah ya kwanta. Washe gari ma haka ya tafi ya ringa yawo garari da ummita yana dan kama aiki ana basa abinda zai siya mata abinda zataci saita rage yaci wani lokacin kuma ruwa kawai yakesha ya dawo su kwanta. ****rayuwa tai masa tsananin gaske dan kuwa daga shi sai ummita suke rayuwa yayi yawon neman umma har inda bai kamata suje ba sunje ba labari dan haka ya maida hankali sosai gurin tattalin Ummita wadda ita kadaice hope dinsa na rayuwa a yanxu,sbd ita ya dage yafara gwagwarmaya da rayuwa, Tin dafe idan suka fita da ita yake yawon aikin wahalar dayake fama dashi se dare suke dawowa su shige su rufe gari na wayewa suke fita sai kuka wani dare. Wahalar rayuwa yakesha sosai ga kulawa da ummita wadda ya kasa barwa ko mama sakina sbd tsoron bazai iya rayuwa ba ummitan a tareda shi ba dan haka yake gwagwarmayarsa da ita a gefensa duk da tafara qara wayo sosai kuma itama bata iya rabuwa dashi ko nan da can dan hakama sbd bata tsaro da kariya ya aske mata kanta daman batada yan kunne ya siya mata kayan gwanjo na maza ya maidata namiji sunanta kuwa kwata kwata baya fada cikin mutane kaman yanda ya hanata magana a cikin mutane sbd muryanta. Ana cikin ya fara examsa dinsa dan haka tare suke zuwa makaranta ya zaunar da ita bakin window dayake ganinta har a gama ya fito ya jata su tafiyarsu gurin yawon nema. Rayuwa tayi musu nauyin da duk kansa yafara neman kuncewa amma ya riqe sbd Ummitah dayayiwa kansa alkawarin inganta rayuwarta bazai bari insha Allah ta taso cikin qunci da azabar daya taso a cikinta ba, Shine uwa kuma ubanta dan haka ko rayuwarsa zai iya siyarwa dan inganta tata. ***Ummita a tata rayuwar batada wani hasken data sani bayan BAABAH dinta wanda shi kadai ya isheta rayuwa, ya isheta jin nutsuwa da ganin haske arayuwar ba duhu ba, Shine uwa kuma ubanta wanda take ganin indai gashi bata buqatan komai hakama shi kadai ne abinda take buqata a rayuwarta. Daqyar ya kammala exams dinsa sbd babu lokacin zuwa aiki dan haka abincin dazai bawa ummita bama kansa ba yake musu wuya dan haka koda aka gama exams din yayi wani irin rama daga shi har ummitan sun bushe dan haka yana gamawa ya duqufa aikin kamfanin daya sake samu da tsaron shago yana hadawa biyu sai suka fara daidaituwa. Ahankali abinci yafara wadatarsu kullum sunaci su koshi ya siya mata abubuwan buqata da nasa ma. Ya siya musu katuwar fitila basa cikin duhu ko kadan yanxu, Ya siyawa kansa waya yar qarama sbd jamb daya rubuta da kuma jiran kiran fitowar jarabarsu. Rayuwarsu tafara daidaituwa shine malamin Ummita na karatun addini harma dana bokon dan haka tafara koyan karatu a gunsa kuma tana ganewa sbd yanada qwaqwalwa sosai dan duk tsananin rayuwar da suke ya tsaya ya samarwa kansa ilimi sbd burin dayake dashi akanta. Mama sakina na cikin tsanani a gidan aurenta sbd baba ila daya tsaneta gaba daya tinda ta kasa cire su abdul a ranta duk ta rame ta qare akan tinaninsu da rayuwar da suke wadda bata cikin nutsuwa da kwanciyar hankali kwata kwata sbd Abdul rayuwarsa ta qare ne akan kulawa da ummita hakama bazai tabbata boyeta a amtsayin namiji na sbd girmanta idan yazo zai nuna hakama tayaya zaici gaba da iya kulawa da ita shi kadai dan haka take cikin damuwa me tsananin gaske da kuma batan Fatima daya tabata itama ta rasa kwanciyar hankali kwata kwata. Baba ila gaba daya ficewa tai a ransa sbd babu dadin zama da ita tinda ta saka ranta a qunci sbd yayan da ba ita ta haifa ba,uwarsu ta tsallakesu ta gudu sai itace zata kawo masa qunci gidansa sbd su duk tabi ta bushe babu komai a jikinta hatta gatanta jin yayi ya bushe masa dan haka ta fice masa kwata kwata a rai ko abincin ma seya dena bata azaba kawai take sha a gidan da baqin ciki tareda hantara da tsana da gori. Abdul bai taba zuwa ko sake barin hanyama ta hadasa da yan uwan babansu ba sbd babu abinda yake buqatan dayafi kada Allah ya hadasa dasu harsu bar kauye dan haka kwata kwata baya hulda da mutane ko shiga mutane sosai kaman iyayensa ya killace kansa daga shi sai kanwarsa wadda itace tafi masa duk wani abu dayake duniyar nan. A gurin aikinsa ahankali yafara zamowa abin kaunar kowa sbd nutsuwa da kamun kansa da kuma maida hankali kawai akan aikin daya kawosa. Tamkar yanda mahaifinsa yake da farin jini da kwarjini haka yafara cika idanuwan mutane duk da shine qaraminsu a kaf ma'aikatan gurin hakama sbd rufin asiri daya fara samu da cimar safe rana dare sai yafara zamowa lafiyayyan saurayinsa wanda haskensa na bafulatin asali suka fara fitowa sosai. ****examsa dinsu ce ta fito wadda tayi kyau sosai kusan fiyeda ta kowa a makarantarsu dan haka yake cikin farin ciki. Rayuwarsa ta qara zamowa akan tsari ne a lokacinda ya samu admission dinsa a university of lagos wadda acan ya cika sbd yanason koyan gwagwarmayan nema, A daidai wannan lokacin ne baba Ahmed ya kawo musu ziyara sbd rasuwar da me gidansu yayi dan yazo ya tafi dasu da takardar da akai ta kudinsu da zai basu zuwa abuja. Sam Abdul bai nuna ummita mace bace a haka suka tafi har abuja bayan tafiya me tsayi suna isa aka saukar dasu gidan wani dan uwan baba Ahmed wanda yake gadin wani gida da babu kowa a cikinsa. Sai washe gari suka isa gidan alh kabeer inda babu wahala bayan sunyi gaisuwa daman ansan da zuwansu babban dan Alhajin ne ya nema Baba Ahmed sbd takardar da dad dinsa ya basa a hannunsa tasu Abdul din dan haka ba wani wahala aka basu dukiya me yawan gaske. Kafin su tafi kwanansu shida a abuja Alhaji Sa'ad 'dan Alhaji kabir din yaji kaunar Abdul kaman yanda dad dinsa yaji yana kaunar Ayouba a can bayan dan haka bae bari sun tafi ba yai masa tambayoyi yaji yana shaawar sakasa a business dinsu sbd Alhaji Kabir ya rasu bayan doguwar jinya wadda sanadin businesses dinsu ne da sukai qasa sun karye sosai dan haka ciwon zuciya ne da Diabetes ya kwantar da Alhaji wanda sukaita yawon kasashe sauran dukiyar duk ta qare daga qarshe koda ya rasu basuda wani abin daya dage musu bayan gidan da suke ciki a yanzu. Amma sbd sauke nauyi da biyan haqqi ya sakasu saida duka motocin gidan suka hada kudin da dad dinsu yayi alkawarin bawa su Abdul wanda yake ganin haqqinsu ne dole ya basu suka nemesu dan basu, Amma ganin nutsuwar Abdul din wanda idan suka basa duka kudin zasu koma ko abinda zasu juya basuda shi gashi shima Saad shi kadaine namiji a gidan sauran kannensa duka mata ne sai mahaifiyarsu dan haka ya gabatarwa Abdul kalar business dinsu na companies din shigowa da manyan qarafunan manyan motoci daga kasar waje da kuma kamfanin Qera nasu da suke dashi tareda bayyana masa komai na business da kuma yanda ake tafiyar da huldodin duka a gaban baba Ahmed da lawyer dinsu. Abdul daman bai saka kudin a ransa ba bare saka lissafinsu a ransa dan haka yace ya bar musu amma a saka baba Ahmed a cikin huldan ya basa kaso daya a bisa uku na dukiyar shima ayi dashi. Gabaki daya familyn gidan jin farin ciki da tsananin kaunar ABDULAZIZ sukai musamman Alhaji Saad dayaji ABDULAZIZ ya zama kaman wani savior dinsu. Baba Ahmed ma jin yayi yana zubarda hawayen farin ciki sbd yana cikin gararin rashin aikin yi shima sai wahalar rayuwa yake sha shiyasa kunyar su Abdul din ta hana ya fito ya taimakawa rayuwarsu. #MAMUH #LIMBAS #ZADEENS #BESTLOVE ZAFAFA BIYAR KALBIM 500 mamuhgee A DUNIYATA 500 Huguma AJIYA A DUHU 500 Billyn Abdul KIRJIN ME HANKALI 500 Miss xoxo Pay at 0022419171 AccessBank Maryam sani gummi Shedan biya 09033181070 Or mtn vtu at 09032345899*_Arewabooks@Mamuhgee_* 10 *ZUZEAM VENTURES* Best APHRODISIAC 08144015291 Aslm barkanmu da wannan lokaci Ina Mai farin cikin sanar daku cewa Zuzeam ventures takawo maku ingantattun magunguna masu inganci cikin Aminci Muna da kaya kamar haka Mallaka Maganin sanyi Maganin cire tumbiMaganin farin jini Maganin matsiMaganin mata Maganin sa ni’ima da dandano Dulka Amare Set na gyran jiki Set na amarya Tabaje tsumin Gomba Xuma kiba ta hips and Brest Magungunan gyran Brest Magungunan Karin hips Maganin sliming Muna da kaya masu inganci  cikin sauki da rahusa Ina wadda keneman mallaka sahihiya quaranty wlh hajiya kixo ga zuzeam ventures xakiji ddin mallaka duk fadin ran ogah duk fadansa wlh sai yyi sanyi 08144015291 Idan maganin mata kikeso akwai Idan gyran jiki kikeso gyran fata gyran Brest magungunan sa kiba da hips DOMIN samunta Kai tsaye kira wannan no 08144015291 DOMIN mgn da ita whatapp 08144015291muna tura kayanmu ko ina cikin iKon allah 🥰👌🏻 Bononza Bononza Tsimin mangoro 1k🥭 Tsimin dabino 1k Gumba ukku balai 700 Gumba aya da nonon rakumi 700 Garin kafi ciccibi 500 Garin bata gaban kishiya 500 Matsin mallaka tada zaune tsaye 2500 Turaren mallaka ba aba mai kishiya 2500 Total kayan 9500 Za a bakisu akan 3800 Kuma mutun goman farko nadakyautar Abun 2k 🗣️🗣️🗣️🗣️🗣️🗣️ ASSALAMU ALAIKUM ALHAMDULILLAH YAN UWA  NEW PROMO YA KAMMALA💃🏽💃🏽💃🏽😁😁😁 da 5k dinki ki kwashi kayan 12k hajiyata 💃🏽💃🏽💃🏽😃🙃Kazar gadali ta mallara Rabi 3500 Tsimin gam gam 1500 Ruwan kara zunzurutun dadı😋800 Garin 7in1 1k Gumba 3 balai 500 Gumba kwakwa da dabino 500 Infection ruwan tsarki 1k Garin zunzurutun dadi 1200 Matsin ba a fira d wando 500 Matsin infection mai matse mace gam 500 12k All at 5k kedai dannan link dinnan don samun naki ki maza kiyi bucking koda kudinki saida Rabonki ******* Lawyer ne a gaban kowa yayi drafting komai da yawan adadin kudin da date da cikakken sunansa ABDULAZIZ AYOUB LIMBA sai sunan Saad din da baba Ahmed kowa ya saka hannu. Anan aka saukesu suka baro gidan dan uwan baba Ahmed akai musu Kyakkyawan sauka wanda anan gidan ne aka gane Ummita mace ce dan haka umman gidan taiwa ABDULAZIZ din karfin halin rabasa da Ummitah ta dawo da ita cikin gida gurinsu. Sosai suka ringa kulawa da Ummitah da tattalinta babu qyama tareda siya mata yan kayan sakawa aka gyara mata hujin kunnanta da harya rufe. Satinsu hudu a abuja suka tattara suka dawo duk yanda Saad yaso ABDULAZIZ ya zauna anan abuja cewa yayi aa sbd makaranta da zai tafi bazai iya barin ummita anan dinba ya tafi karatu yabarta a gurin wainda bai saniba. Bayan tafiyarsu suna dawowa gida da kwana biyu yaje ya sanarwa mama sakina karatu zai tafi. Tashi hankalinta yayi mummunan yi sbd batasan tayaya ABDULAZIZ din zaiyi tinanin tafiya da Ummitah karatu ba har nesa dan ita batama san lagos din ba a baki suke jinta. Shi kansa ABDULAZIZ din yana cikin tsananin damuwa da tashin hankalin yanda zaiyi sbd shi kansa bazai iya zuwa da ita inda yasan ba tsaro ba gwagwarmaya me kalubalen gaske. Damuwar hakan ce ta sakosa gaba ya koma kalar tausayi damuwa me karfin gaske ta shigesa, Daga karshe yafara tinanin fasa tafiya karatun sbd Ummitah sbd ta fi masa karatun zai zauna ya reneta. Wannan shawaran daya yanke ta fasa karatun ya hakura dashi ya saka mama sakina shiga damuwa me tsananin data sake dagula dan zaman datake a gidan baba ila tsangwamar dayake mata tai yawan data saka ciwo kwantar da ita sedai ta kasa samun Sassaucin damuwar datake ciki na fasa karatun ABDULAZIZ din dan haka dataga babu sauyi ABDULAZIZ din ya hakura da karatunsa harya fara aikinsa kwana tayi tana kukan data kasa riqewa tana tina fatima da gatan da aka haifi a Abdul din a cikinsa har safe tana kukan daya sakata qarasa ficewa hayyacinta karshe ta hakura ta sadaukar da aurenta tayiwa baba ila maganar zata karbo Ummitah ta dawo da ita hannunta ABDULAZIZ zai tafi karatu. Sadaukarwar datai da shahadar masa magana tasan ta tashin hankalin da zata fuskantace tareda Ummitan a gidan dan ko abincin da zasuci ta sani sedai ta fara nemar musu shi da kuma kaurace mata da kila baba ilan zaiyi gaba daya daman ya dade da kaurace mata kumata shirya hakan dan haka tai sadaukarwartai masa magana sedai babban abinda bata zata ba shine kai tsaye tana kai karshen zancenta yace ya saketa saki uku ta tafi can gaba tayi riqon Ummitan. Dagowa tayi da jajayen idanuwanta na kukan data kwana yi ta zuba masa tsawon mintina tana kallansa harya wuce daga kofar dakinta ya fice daga gidan. Wasu hawaye ne masu tsananin zafi da ciwo suka gangaro mata ta rintse idanuwanta tana kasa dagowa saiga wani irin kuka me ciwo ya kufce mata zube a gurin tanayinsa ba sauti. Ta jima a gurin kafin ta miqe ta shiga dakinta ta tattaro yan kayanta da duka buhu daya ne zai dauke mata su sbd ko katifa batada ta siyar tin gurin taimakawa su fatima dan haka tabarmace kawai tsohuwa sai sanin shimfida daya da kayan sawarta da basu fi kala uku ba sai kwanonin da tini suka mutu tin na aurenta shekaru kusan ashirin harma da dori dan haka tana hada kayanta a buhu ta fito taje kuryan gidan tayiwa yan gidan bankwana ta fito suna gulmanta ta fice. Kai tsaye gidansu ABDULAZIZ din ta nufa. Basa nan dan haka tinda gidan ba kofane dashi ba ta shiga ta ajiye kayanta ta nemi guri ta zauna. Sai yamma sosai suka dawo Ummitah na ganinta tazo gurinta da gudu ta rungumeta tana cewa "Maama" ABDULAZIZ kayanta ya kalla ya kalli fuskanta take ya fahimci abinda yake faruwa dan haka baice komaiba sannu da zuwa yai mata yana fada mata abinda suka tsaya yi sukai yamma. Ummita kallan Maman tayi tana cewa "Mamah anan zaki kwana?? Murmushin karfin hali da boye damuwa mamah tayi tana cewa "Eh yanzu na dawo dake zan ringa kwana kullum muna rayuwa sbd Baabanki ya tafi karatunsa, Ai zaki yadda ya tafi ko?? Juyawa tayi ta kallesa yana alwala a natse kafin ta dawo da kallanta akan maman tace "Eh zan yadda sbd BAABAH na son karatu ya fada a waya naji" Ajiyar zuciya maman ta sauke sbd tasani idan Ummitah tace bata yaddaba to har abada yabar karatun. Yana gama Alwala masallaci ya wuce sbd maman na tareda Ummitah. Baa cika ganinsa masallaci ba sbd acan gurin aiki yake wuni dan haka a masallacin can suke sallah magriba kuma koda yake isowa gida anyi wani lokacin kuma jam'in waje yakebi sbd Ummitah sallar asuba kuma a gida yake binta sbd ba tsaro ya fita yabar Ummitah sbd akwai bata gari ko barayi. Ayau ganinsa masallaci ya saka kawunninsa mamaki sedai ko alaman ganinsu baiyiba sbd bayama gane kamanninsu sbd rabonsa da ganinsu yama manta tin yana karaminsa. Saida yayi ishai ya dawo gida sbd saida yayi karatun qur'ani. Koda ya dawo maman ta dafa musu shinkafa da mai da yaji dan haka ya zauna a tsakar gidan sukaci suna gamawa yayi kwanciyarsa a kofar dakin da tabarman maman datazo da ita ya kunna maganin sauro guda biyu ya zagaye kansa dashi yabar musu dakin sbd gidan dakin daya ne tini ya rage sauran sun zube. Washe gari gurin aiki ya tafi yabarsu gida ummita nata murna sbd mama zata zauna dasu. Se dare ya dawo sbd baya tareda ummita daman sbd ita yake dawowa da wuri. Tuwo ya samu anyi sbd yanada abinci a gidan sukaci suka koshi a daren ne sukai magana tace ya tafi karatunsa ita kuma zata koma gida gurin innarta da Ummitah sbd idan ma sun zauna anan zaaita tsangwamarsu ne hakama tinda an rena gidan ba kofa a bude yake idan bayanan zaaita musu sata ko wani abin ma dan haka zata koma can garin gashi a hade yake da local government. Naam yayi da hakan shika tareda samun nutsuwa da zancenta dan haka ya amince sbd yasan kaunar da ummansu zataiwa Ummitah dama wadda batai mataba maman tanai mata dan haka zai tafi yayi karatu da nema dan inganta rayuwarsu su biyun da Ummitah da maman wadda a yanxi itama ta zama tasu nauyinta ya hau kansa kaman yanda na uwar data haifesa zai hau kansa. Washe gari yafara shirin tafiya makaranta wanda ba wani shiri bane kudadensa dayake tarawane kawai da wanda ya bawa me gidansa na baya ya zuba a shago yaje ya karba ya dan yiwa su Ummitan siyayyar omo da sabulun wanki da mai se panties da vest da brush da macleans daya siya musu sai kuma abimci daya shiya musu me dan dama dama. Kwana biyu suka gama shirin komai suka nufi garin mahaifiyarsa wanda shine garin mama sakinar. A gidansu sakina koda suka iso baba ila tini ya kawo zancen tareda duka munanan illoli akan sakina wanda ya saka yam gidansu dayake gidan taro tsanarta tin kafin ta iso ita da 'yartata wanda kowa ya sani ba wanda ya isa ya rabata da ita tinda ansan irin yanda take da fatima dan haka ba wanda ma zaice zai rabata da jinin fatima sedai kuma kwata kwata basuyi maraba da dawowanta ba. Innarta kuwa da tsufa ya kama sosai kusan batada karfin komai amma ita kam tayi maraba da 'yayan fatima sbd kaunar dake tsakanin fatima da sakina tasan daga Allah ne hakama Allah ne kadai yasan dalilinsa na hanawa sakina haihuwa yabar mata yayan fatima. Koda suka iso kai tsaye bayan angama gaisawa da jamaa bangaren inna dayake dauke dauke da dan qaramin tsakar gida da daki daya sai bandaki da rumfar girki sai dakin kiwon kaji da yar tinkiyarta suka shige. Dakin ba tarkace sosai dan haka suka zauna anan suka dawo da zancen komai baya suka tattauna kafin mama tai masa nasihar riqe gaskia da kaucewa haram komai kankantarta idan ya tafi can. Ummitah tinda suka taho tana jikinsa ta lafe tanajin anfara maganar tafiyarsa tafara hawaye tana qanqamesa. Jajir idanuwansa sukai shima sbd tinda aka haifeta baitaba rabuwa da ita ba sai yanzu. Rarrashinta aka fara amma sai hakan yafara tayar mata da hankali tafara rikice musu tana fasa kuka me karfi tana sake riqesa da karfi. Kasa banbareta daga jikinsa yayi yana kokarin dago fararen idanuwansa da sukai jajir ya zuba mata yana zuciyarsa na nauyi. Rikicewa tayi gabaki daya tana musu ihu da kukan daya saka duk jamaar gidan fitowa cikin mamaki da tsoro sbd basu saba ganin hakan ba. Mama sakina ganin yanda Ummitan ta haukace gaba daya ta fice hayyacinta take ya sakata fara kukan itama, Inna ma kukan ta fara hakama duk yan gidan da suka shigo bangaren sanyi jikinsu yayi sbd kallo daya zakai musu ka tabbatarda wata irin kaune ce tsagwaronta babu sarki. Rungumeta yayi qam a jikinsa tsawon mintina yana tofa masa addoin samun nutsuwa dana kariya daga sharrin duk wani sharri kafin ya zareta jikinsa da karfi yasakata jikin mama sakina data qanqameta da karfi. Kudi ya ajiye musu mara wani yawa ya juya ya fice idanuwansa a qasa sbd jan da sukai ya fice gidan. Se dare ya iso gida ya zauna wasu hawaye masu zafi da radadi sika gangaro masa ya rintse idanuwansa yana adduar Allah ya tsare masa Ummitah daga sharrin komai dayake duniyarnan har lokacinda zai karbeta ta dawo hannunsa. Tinda dare ya tsala yake zaune akan abin sallah yanawa rayuwar Ummitah da tasa tareda iyayensa wanda mama sakinana ciki addua har asuba. Wanka ya fara yi kafin yayi alwala yafice masallaci sallah sbd a lolacin aka tada. A masallaci yana fitowa ya hade da kawunninsa biyu wanda suka kallesa amma sam baima dagoba bare ya kallesu sbd Allah ya haliccesa da wata irin kafiya akan abinda yake qi koya tsana hakama kafiya akan abinda yake tsananin so da kauna dan haka idan ya tsani abu to har abada bayajin zai taba kaunarsa. Su kansu sunsan yanada kafiya da taurin zuciyar da bazai taba ko kallansu ba. Yana isa gidan daman ya hada komai nasa dan haka jakarsa daya siya ya saka yan kayansa daya siya ya dauka ya goya a bayansa ya tattara komai nasu ya ajiyegefe ya fito ya rufe dakin ya saka padlock ya rufe ya juya ya fice gidan. Yana fita ya hau keken wani abokin aikinsa daya hadu dashi a hanya ya kaisa har hanyar mota daga can ya hau mashin zuwa tasha. Yana isa ba jimawa motarsu ta cika suka daga zuwa abuja inda acan zaibi motar lagos. Sai dare suka isa abuja dan haka baima bari gidansu Alh Saad suka san yana abuja ba yakwana a tasha karfe dayan dare motarsu ta tashi zuwa lagos. #MAMUH #LIMBAS #AZIZ LIMBA ZAFAFA BIYAR KALBIM 500 mamuhgee A DUNIYATA 500 Huguma AJIYA A DUHU 500 Billyn Abdul KIRJIN ME HANKALI 500 Miss xoxo Pay at 0022419171 AccessBank Maryam sani gummi Shedan biya 09033181070 Or mtn vtu at 09032345899 *_Arewabooks@Mamuhgee_* 11 *ZUZEAM VENTURES* Best APHRODISIAC 08144015291 Aslm barkanmu da wannan lokaci Ina Mai farin cikin sanar daku cewa Zuzeam ventures takawo maku ingantattun magunguna masu inganci cikin Aminci Muna da kaya kamar haka Mallaka Maganin sanyi Maganin cire tumbiMaganin farin jini Maganin matsiMaganin mata Maganin sa ni’ima da dandano Dulka Amare Set na gyran jiki Set na amarya Tabaje tsumin Gomba Xuma kiba ta hips and Brest Magungunan gyran Brest Magungunan Karin hips Maganin sliming Muna da kaya masu inganci  cikin sauki da rahusa Ina wadda keneman mallaka sahihiya quaranty wlh hajiya kixo ga zuzeam ventures xakiji ddin mallaka duk fadin ran ogah duk fadansa wlh sai yyi sanyi 08144015291 Idan maganin mata kikeso akwai Idan gyran jiki kikeso gyran fata gyran Brest magungunan sa kiba da hips DOMIN samunta Kai tsaye kira wannan no 08144015291 DOMIN mgn da ita whatapp 08144015291muna tura kayanmu ko ina cikin iKon allah 🥰👌🏻 Bononza Bononza Tsimin mangoro 1k🥭 Tsimin dabino 1k Gumba ukku balai 700 Gumba aya da nonon rakumi 700 Garin kafi ciccibi 500 Garin bata gaban kishiya 500 Matsin mallaka tada zaune tsaye 2500 Turaren mallaka ba aba mai kishiya 2500 Total kayan 9500 Za a bakisu akan 3800 Kuma mutun goman farko nadakyautar Abun 2k 🗣️🗣️🗣️🗣️🗣️🗣️ ASSALAMU ALAIKUM ALHAMDULILLAH YAN UWA  NEW PROMO YA KAMMALA💃🏽💃🏽💃🏽😁😁😁 da 5k dinki ki kwashi kayan 12k hajiyata 💃🏽💃🏽💃🏽😃🙃Kazar gadali ta mallara Rabi 3500 Tsimin gam gam 1500 Ruwan kara zunzurutun dadı😋800 Garin 7in1 1k Gumba 3 balai 500 Gumba kwakwa da dabino 500 Infection ruwan tsarki 1k Garin zunzurutun dadi 1200 Matsin ba a fira d wando 500 Matsin infection mai matse mace gam 500 12k All at 5k kedai dannan link dinnan don samun naki ki maza kiyi bucking koda kudinki saida Rabonki ********* ******** A lagos kai tsaye Alh saad yai masa registration daman hardana hostel da komai tini daman aka basa takardun komai suna hannunsa dan haka yana isa wanda Alh saad ya basa numbernsa ya kira suka hade yakaisa har hostel har cikin dakinsa. Shima students ne wanda aka hadasa dashi dan haka washe gari shiya zo ya jasa suka qarasa sauran registration dinda baa qarasaba da sauran abubuwan. Kwanaki ya dauka Muhammed yana nuna masa komai na makarantar da yanda zai muamalanci mutane da Guraren lectures da da komai seda ya dan fahimta tukuna Muhammed ya kyalesa duk da kusan kullum suna haduwa. Karatu da rayuwa a cikik kabila da kuma mutanen da bama ka saba ganin irinsuba abu me tsananin azaba da wuyar gaske tareda gajiyawa musamman dayake akwai kabilanci sosai da banbancin rayuwa sai abin yaso yai masa nauyi, Amma kasancewansa wanda ya taso gwagwarmaya da tsananin rayuwa tareda rashin sabawa da muaamala da mutane sosai sai hakan bai dade yana wahalar dashiba ya bada himma kawai gurin karatu da dan aikin daya fita da kansa ya nemowa kansa a wani shagon hada lalatattun computers wanda yake samun dama biyu ana biyansa kuma yana koyan computer tareda saninta sosai. ******karatunsa yayi nisa ahankali kaman yanda aikinsa yayi nisa sbd acikin qanqanin lokaci ya zama dan gari ya samu zama babban me kulawa da office din computer din hakama karatunsa sosai yake tafiya yanda yakeso duk da akwai wahala amma ya dage sbd AERONAUTICAL ENGINEERING  ne yake karanta wanda karatune dayayi focusing akan development da production of aircraft. Aiki yake sosai da business tareda karatu wanda ya sakasa sauyawa a kankanin lokaci sbd rufin asiri dayake cikinsa sosai. Shekara guda ya share cur bai tafi gida ba sbd yanayin aikinsa dayake shine yake kulawa da komai gashi yana karatun sosai harma dana addini dan haka waya kawai yakeyi sosai dasu Ummitah wadda tafara zamowa yan mata. Koda zai taho ganin gida siyayyar da yayi musu saika dauka shagon sayarda kaya zai bude musu a kauyen dan ko takarman sakawan Ummitah da maman zasu kai kala goma goma koma fiye hakama kayan sakawan ummita da panties ma kadai dozen uku ya siya mata sai singlet da small small hijabs da kayan shafa da turaruka, Akwati ma guda biyu ya siyo musu manya na saka kayan, A taqaice kaman wanda zaiyi aure haka ya hado musu lafiyayyan lefen kaya ya biyo hanya, Saida ya sauka a local government ya siya abinci shima kaman hauka ya dauki mota guda da kayan ya nufi gidan. Ummitah na islamiya ya iso dan haka da gudu akaje aka sanar mata Kallan wadda ta fada mata tayi da kyau da fararen idanuwanta masu shegen kyau da haske wanda suke kama sak da nasa tace "HAMMAN UMMITAH ne kin tabbata ya dawo? Idan bashine ba kikasa na tafi fada zamuyi" Da sauri yarinyar tace "Eh shine da kaya sosai da mota yazo" Shiru tayi tana shiga bugawar zuciyar sbd Hamman Ummitah kaman yanda take kiransa yanzu ne to ko sunansa aka fada bugawa zuciyarta takeyi sbd tsananin farin ciki shiyasa ake tsokanarta da cewa yazo. Allonta dayake hannunta ta ajiye gefenta ta miqe bata tsaya komaiba ta falfala da mugun gudu tabar makarantar. Tin daga nesa ya hangota a guje tana zuwa daman shima tin dazu ana sauke kayan idanuwansa n hanyar makarantar kaman zuciyarsa zata bude sbd tsananin buqatan ganin hasken idaniyarsa farin cikinsa bugun zuciyarsa kuma. Dan haka yana hangota idanuwansa sukai wani irin sanyi zuciyarsa na karba itama hakama gangar jikinsa da duminta kawai yake buqata a jikinsa ko zai samu karfin mutuwar da jikinsa yayi na rashin ganinta. Daidai lokacin mama sakina ta fito daga gida da sauri itama cikin tsananin farin cikinda batasan yaushe ta fara hawayen ganinsa ba. Hannuwansa ya warewa Ummitah yana tafiya zuwa gareta daidai tana isowa da gudun gaske ta fada kansa yayi sama da ita ya rungume da tsananin karfi yana sauke ajiyar zuciyar dayayi shekara nawa bai saukeba idanuwansa na kadawa zuwa ja. Itama qanqamesa tayi tana fasa kukan farin ciki tana jin kaman ta bude cikinsa ta shige sbd tsananin kewa da kaunar datake tsakaninsu. Sun jima a hakan anata kallansu wasu na mamakin irin tsananin so da kaunar dake tsakaninsu wasu kuma na tausaya musu wasu kuma na gulman yanda ya rungumeta. Kasa sauketa yayi duk da tafara girma ahaka suka juya zuwa cikin gidan bayan angama shigar da kayan mama sakina ma hawayen takeyi ya kama hannunta sukai ciki. Inna ma duk da idanuwanta basa gani tayi farin ciki da dawowansa sbd kunnuwanta zasu huta da rigimar Ummitah idan taso rashin arzkinta kuka take zaunawa ta ringa musu akan saiya dawo. Yan gidan ganin tarin kayan arzikin da akazo dasu ya saka suka ringa shigowa yi masa barka da zuwa harda masu kawo lafiyayyar fura dataji madara me tsafta. Godia yayi musu mama sakina ce ta karba ta ajiye sbd bataga alamar zai iya sha ba sbd ya sauya musu gaba daya ya koma wani ABDULAZIZ din daban. Ummitah datake jikinsa gyara zamanta tayi a jikinsa yana share mata hawayenta da handkerchief dinsa me qamshi yana kallan idanuwanta da hancinsa dasuke sak nasa kaman shine ya haifeta, Tayi haske sosai tama kusan kamosa a haske gata fes fes kusan ta banbanta da yan kauyen sosai sbd ya tsaya sosai akansu yana musu aike sam baya wasa da duk abinda ya shafi cinsu da buqatansu. Mama sakina kuwa sosai take kulawa sa Ummitan harma mantawa takeyi da ba itace ta haifeta ba sbd so da kulawa da tattali dan hakanne ma Ummitah ta banbanta sosai da duk yaran garin ko yayan me gari va abinda suke nuna mata, A bangaren gata da sakartawa kuwa kusan kaf garin babu kamarta sbd mamah ta sakartata sosai gata take nuna mata sam bata mata fa kuma Allah bai saka tafara lalacewa hakama sam bata barinta wani fita wasa ko yawo koyaushe tana killace daga makarantar boko da aka sakata ABDULAZIZ din na aiko kudin me mashin din dayake zuwa kaita ya daukota wanda shima da maman ake zuwa a kaita a dawo da maman gidan hakama idan zaa daukota sai anzo an dauki maman aje a daukota a dawo dasu tare sbd sam bai yadda a ringa daukanta ita kadaiba sbd tsaro da kiyayewa. Dan hakan ne daga makarantar bokon sai Islamiya bata zuwa koina, Kitso da lalle ma idan zaayi mata mamanta ce take kaita ta dawo da ita daga baya ma kudi ABDULAZIZ din yake aikowa idan zaayi sai azo gida ayi mata duk da tana yarinya qarama sai hakan ya saka gaba daya garin Ummitah ta koma kaman wata 'yar sarki. Fira yakeyi da mama wanda kusan itace da inna masu maganar shi kuma sbd bai cika magana ba sai maganarsa take a taqaice gashi gaba daya hankalinsa yana kan Ummitah sbd wani irin kallan nutsuwa da kiyayewa yakewa koina nata sbd ganin tabon rauni daya a bayan hannunta ya sakasa bin koina nata da kallan nutsuwa a natse batareda  kowa ya lura da hakan ba. Mama ta lura da hakan sedai tasan irin tsananin son dayakewa Ummitah bazai nutsuba ganin rauninta dan haka taji shima ta qara tsananin kaunarsa. Ummitah ma dogayen yatsin hannuwansa dake farare tas kaman wanda yake cikin tsananun hutu take wasa dasu tana basa labarin duka abubuwan datake da baya nan da yanda mamanta ke sangartata da tsananin sonta. Inna ce basa shiri sosai sbd yanda Maman ta daurewa Ummitah tana girma amma batada aiki sai kukan banza idan taso dawowan ABDULAZIZ din. Wani irin sanyi zuciyarsa da jikinsa yayi ya dago idanuwansa da suka dan sauya ya kalli mama wadda tai qasa da kanta cikin taushi da muryansa me nutsuwa yace "Mama Allah ya saka da mafificin khairi ya saka da gidan Aljannah" "Amin" inna tace tana jin kaunarsu dukansu kaman jikokinta na jini da sakina ta haifa. Mamar kuwa ajiyar zuciya ta sauke tana bude baki tace "ALLAH yai muku albarka ya baku kariya da arzikin da bayajin kashewa yai maka budi ya daukaka rayuwarka ya baka duk abinda kake nema duniyar nan yaji qan iyayenku ya tsareku daga sharrin duk me sharri" Amin" ya amsa dashi a sanyaye yana dorawa da godia. Abinci lafiyayye maman tayi masa tabarsa yana fira da Ummitah datake ta faman yamutsashi tana basa labarai kala kala yana saurarenta sbd sautin karatun Al'qurani ne kadai yafi masa dadin muryanta da labaranta dan haka wani sanyayyan murmushi ne da babu me gani a fuskansa yake mata yana kallan bakinta yana tina ummansu wadda ita mama ta maye mata gurbinta sbd yanda ya lura tsananin so takewa maman nata shi kuwa har abada bayajin gurbin dayake zuciyarsa na kewan ummansa zai cike sbd yanada qawa zucin mahaifiyarsa duk da mama sakina maye gurbi me yawan gaske a rayuwarsu da kusan yake jinta kaman uwar data haifesa. Kiran magrib da akai ya sakasa fitowa sukai alwala tareda Ummitah tukuna shi ya fice zuwa masallaci ita kuma tayi sallah tareda mamanta. Yana dawowa aka jere masa abinci a tsaftacen guri tareda sabuwar tabarmar da maman ta siya sbd zuwansa kawai dan haka ya zauna. Tareda Ummitah yaci abincin kusan ma duk ita ya tsaya kalla tana cin abincin saida ta koshi kafin shima yaci wanda ta rage sbd ragin nata yakeson yaci sbd son dayake mata irin wadda ko qazantarta abar tsananin so ce garesa, haka kawai wani lokutan idan ya zuba mata ido yana kalla sai yanajin idanuwansa na sauyawa zuciyarsa na sanyi sbd jin kaman ya maidata cikinsa ya adana daga sharrin duniya dana mutane, Tsananin So ne me tsafta da babu sirki irin wanda uwa da uba kewa 'dan dasuka haifa yake mata sbd jin yake kaman a tsatsansa ta fito tinda shine uba kuma uwarta, A hannunsa aka haifeta,shine ya reneta,shine wankanta,fitsarinta da kashinta ma,shayarwa ne kadai mahaifiyarta tai mata dan haka bai sauke kansa daga uwa kuma ubanta ba. Har dare sosai yana gidan saida tayi bacci a jikinsa tukuna yayi musu saida safe yabar gidan yakoma local government da daman yariga ya kama gurin bacci kayansa ma nan dan baima da niyar zuwa garinsu. Wanka kawai yayi ya sauya kaya ya saka wayarsa caji ya kwanta yana sauke ajiyar zuciya take yayi baccinsa hankali kwance. #MAMUH #BESTLOVE #AY LIMBAS #UMMITAH LIMBA #JAN ZADEEN #DONOR ZAFAFA BIYAR KALBIM 500 mamuhgee A DUNIYATA 500 Huguma AJIYA A DUHU 500 Billyn Abdul KIRJIN ME HANKALI 500 Miss xoxo Pay at 0022419171 AccessBank Maryam sani gummi Shedan biya 09033181070 Or mtn vtu at 09032345899*_Arewabooks@Mamuhgee_* 12 *ZUZEAM VENTURES* Best APHRODISIAC 08144015291 Aslm barkanmu da wannan lokaci Ina Mai farin cikin sanar daku cewa Zuzeam ventures takawo maku ingantattun magunguna masu inganci cikin Aminci Muna da kaya kamar haka Mallaka Maganin sanyi Maganin cire tumbiMaganin farin jini Maganin matsiMaganin mata Maganin sa ni’ima da dandano Dulka Amare Set na gyran jiki Set na amarya Tabaje tsumin Gomba Xuma kiba ta hips and Brest Magungunan gyran Brest Magungunan Karin hips Maganin sliming Muna da kaya masu inganci cikin sauki da rahusa Ina wadda keneman mallaka sahihiya quaranty wlh hajiya kixo ga zuzeam ventures xakiji ddin mallaka duk fadin ran ogah duk fadansa wlh sai yyi sanyi 08144015291 Idan maganin mata kikeso akwai Idan gyran jiki kikeso gyran fata gyran Brest magungunan sa kiba da hips DOMIN samunta Kai tsaye kira wannan no 08144015291 DOMIN mgn da ita whatapp 08144015291muna tura kayanmu ko ina cikin iKon allah 🥰👌🏻 Bononza Bononza Tsimin mangoro 1k🥭 Tsimin dabino 1k Gumba ukku balai 700 Gumba aya da nonon rakumi 700 Garin kafi ciccibi 500 Garin bata gaban kishiya 500 Matsin mallaka tada zaune tsaye 2500 Turaren mallaka ba aba mai kishiya 2500 Total kayan 9500 Za a bakisu akan 3800 Kuma mutun goman farko nadakyautar Abun 2k 🗣️🗣️🗣️🗣️🗣️🗣️ ASSALAMU ALAIKUM ALHAMDULILLAH YAN UWA NEW PROMO YA KAMMALA💃🏽💃🏽💃🏽😁😁😁 da 5k dinki ki kwashi kayan 12k hajiyata 💃🏽💃🏽💃🏽😃🙃Kazar gadali ta mallara Rabi 3500 Tsimin gam gam 1500 Ruwan kara zunzurutun dadı😋800 Garin 7in1 1k Gumba 3 balai 500 Gumba kwakwa da dabino 500 Infection ruwan tsarki 1k Garin zunzurutun dadi 1200 Matsin ba a fira d wando 500 Matsin infection mai matse mace gam 500 12k All at 5k kedai dannan link dinnan don samun naki ki maza kiyi bucking koda kudinki saida Rabonki ********** Washe gari bai tafi gurinsu ba sai bayan azahar ya biya ya siya musu kaji lafiyayyu guda biyu da fruits ya taho. Koda ya iso Ummitah tanata yawon kofar gida da jiransa sbd tana tashi bata gansa ba taso daga musu hankali inna ta tashi tsaye akanta akan karma ta fara musu borin data saba. Mamanta ce ta ringa lallabata har suka samu ya iso bata rikice musu ba. Yana zuwa tayi kansa da gudu ta maqale dan ita shi take damuwa dashi ba kayan dayazo dasu ba. Ciki suka nufa ya miqawa mama kayan hannunsa yana dauke da Ummitan da hannu daya mama na mamakin yanda bayajin nauyinta ko kadan. Abinci sika ci tare tareda fruits daya saba da cinsu sbd sune suka fara zama abincinsa acan sbd farko farkon zuwansa yayi fama da yunwa da dan rashi kafin ya samu abinyi dan haka su yake siya na kudi kadan yasha ruwa ya kama kansa shikenan shiyasa suka shigesa. Suna gamawa aka sauya mata kaya tarin kayan daya siyo mata ta saka hijab me kyau da takarmi da turare suka fita. Suna fita mama sakina ta fidda kayan ta sakawa Ummitah nata a akwati dakyar ya rufe itama nata sakawa tai a akwatinta daya siyo musu ta rufe inna ma takarma da atampa biyi da tirare ya siyo mata dan haka tsofin kayansu da tarin sabulai da omo daya siyo musu ta ringa rabawa yan gidan da moqota tsarabar Hamman Ummitah wanda take aka ringa jin kaunar Ummitah da hamman nata. Yawo suka tafiyarsu can local government yaje da ita masaukinsa ya siya mata kayan ciye ciye sukaita yawo harda saloon ya kaita akai mata harma da wankin kafa. Se yamma sosai sika dawo bema zauna ba ya juyo. Naman kajin ma da mama ta soya tai masa abinci baici ba yace su cinye kawai fresh sabon nono me hade da madaran shanu kawai ya karbo ya tafi dashi ya sha da dare yayi shirin bacci ya kwantawarsa. ****satinsa biyu a garin babu ranar baya fita da Ummitah ya kashe musu kudi sosai ya sake sangartata Kaf garin babu wanda bai jinjinawa girman kauna da shaquwar dake tsakaninsu dan dole ma aka shafa musu lafiya gashi yanada alkhairi sosai sam baida rowa yan garin sun lasa arzikinsa sosai dan haka kowa yanzu kaunar Ummitah yake sbd farin jinin da ABDULAZIZ din yayi a cikin kwanakin kalilan kowa adduar arziki da budi tareda nasara yake masa. Da zai tafi saida akai rigima da Ummitah sosai kafin ya tafi cikeda kewanta yabarsu da kewansa suma. Bayan dawowansa abubuwa sunci gaba da tafiyar masa cikin wani irin nasara da budi dan tini yafara tafiye tafiyen kewayen lagos. Ahankali rayuwa taci gaba da tafiyar masa hakama karatunsa sosai yake tafiya daidai sai gashi har ghana yafara zuwa harkan business din computers. Acan ghana ma yayi mutane sosai, Ta bangaren business dinsu da alhaji saad kuwa komai Allah ya saka musu albarka sosai ake tafiye tafiye kudi na shigowa sosai kuma ganin ABDULAZIZ din yanada wani irin farin jinin aiki ya sakasa fara sakasa a aikin ta can bangaren lagos sai ya zama ABDULAZIZ din baya abuja baya lagos ga karatu da kuma dayan business dinsa dayake habbaka sai ya zama busy sosai bai wani cika zuwa gida ba sai akai akai sedai kullum yana cikin waya dasu dan bai taba bacci ba batareda yayi waya da Ummitah ba wadda itama duk tsananin bacci batayinsa sai lokacin kiransa yayi sunyi waya take bacci. *****lokacin yaja karatunsa yana gap da kammaluwa hakama zuwa lokacin kudi sun fara zauna masa sbd tako ina kudi shigosa sukeyi business dinsa na tafiya hakama na gurinsu saad na tafiya. A shekaran daya kammala degree dinsa a lokacin yafara fita qasar waje tareda saad akan harkan business dinsu dayayi wani irin habbaka hakama ga nasa na daban na harkan computers da aircraft dinsa dayake daukaka sosai kaman ma saurayin matashi ba dan kudi kam suna zaunuwa. Italy suka fara zuwa suka share kusan watanni kafin suka dawo shi ya sauka a ghana shi kuma saad ya wuce abuja. A ghana saida share tsawon lokaci kafin ya dawo lagos tukuna ya wuce abuja acan yayi service dinsa. Da yana service ne yake yawan zuwa ganinsu Ummitah daya sauya rayuwarsu a garin suka koma tamkar taurarin dake haske garin. A garin ABDULAZIZ LIMBA shine tamkar gatansu kuma sarkinsu sbd yansa yake taimakawa kowa yake musu alkhairi dan ya riga ya saba duk abinda zaiyi aike me yawa yake aikowa sbd a rabawa mutane harma da maigari ABDULAZIZ ya zamar masa tamkar wani ginshikin dayake jingina akansa. Alkhairi yake musu sosai sbd kowa na kaunar Ummitansa duk inda ta wuce kowa sonta yake hakan yasa babu abinda bazai iyawa yan garin ba, Ya gina musu islamiya da masallaci me kyau hakama gidansu mama ya koma wani tauraro a garin da babu abinda suka rasa a kauyen. Yana gama service babu bata lokaci ya jona degree na biyu a italy sbd business dinsu dayake tafiya acan sosai dan haka ya tattara yabar kasar ya tafiyarsa. Yaso dawo dasu Mama abuja sbd karatun Ummitah amma sbd baya zaune a qasar yasa yafi samun nutsuwa dasu zauna acan gida cikin family da tsaro kafin yayi settling tukuna dan ko ya dawo dasu baida nutsuwa tinda bayanan hakama suma basu saba da nan dinba zasu shiga kadaici da damuwa dan haka tinda shima baida takamaimai inda yake zaune saiya zabi su zauna acan din kafin ya zauna guri daya. Mashin ya siya aka ajiye na kai Ummitah makaranta me kyau kawai hakama babu abin jin dadin dabai zuba musu ba. Acan italy yana karatu ne tareda business hankali kwance cikin nutsuwa da ilimi da wayewan data shigesa sedai bai sauyaba daga mara son hulda da mutane sosai da hayaniya yana nan ABDULAZIZ AYOUB LIMBA dinsa HAMMAN UMMITAH. Bayan halinda da dabiunsa da basu sauya ba babu abinda bai sauyaba daga garesa, Ya koma wani irin kakkarfan namiji me ji da sabon jini da farin jini da kwarjini me karfin gaske tareda kudi dasuke zauna masa hakama matashin da kyau da nutsuwansa suke sakawa mutane kwarjinsa sosai. A rayuwarsa bayan bautawa ubangijinsa idan gari ya waye geamin ko jogging yake fita kowace safiya Daga can kuma yana dawowa yake wanka yayi breakfast ya fice karatu daga can yana dawowa gurin aikinsa yake wucewa, Wani lokacin kuma aikin yake fara fita kafin ya tafi makaranta daga baya. 4 years ya share a italy ya gama karatunsa tini ya fara aiki me kyau sbd iliminsa dayake fin na abokan karatunsa ko yaushe dan haka yana gamawa ya samu aiki kusan guri hudu masu kyau da girma akaso daukansa aiki amma karshe ya fara aiki a wani babban kamfanin qera jiragen sama kuma a babban matsayin daya sakasa mallakan gidan kansa da motan hawa har biyu. A farkon fara aikinsa kwata kwata babu wata dama ko kadan ta barin kasar yayi tafiya dan haka duk yanda yaso tafiya gida bai samu damar hakan ba seda maman da kanta ta karfafesa akan babu damuwar komai yayi zamansa tinda suma suna lafiya ba matsala ko damuwar komai. Ummitah data zama yar budurwa itama karfafasa tayi akan ya vari saiya samu time tinda idan yazo zai daukesu ne yabar qasar dasu gabaki dayansu. Hakan ya basa qwarin gwiwa da kwanciyan hankali ya nutsu akan aikinsa. Baai wata shida da fara aikinsa ba sukai tafiyan karatun wani program na wani aircraft dazasu hada a kamfaninsa dayake kokarin budewa shima zuwa Sidney. Tinda yayi tafiyar su Mama suka dena samunsa shima kwata kwata ya dena samunsu sbd wayarsu da aka sace daga zuwa bikin wata yar gidan da aka aurar aka kai binni sukaje kai amarya. Sun siya wata wayar amma tsautsayi da kaddara suka hana Ummitah haddace numbernsa sbd kullum cikin yawon kasashe yake numbernsa ba daya bace dan haka bata haddace numbernsa ta Sidney dinba sabanin sauran numbers nasa data haddace dan haka communicating ya yanke a tsakaninsu kwata kwata. Sun shiga damuwa da tsoro sosai wanda ya saka Ummitah komawa wata sanyi sanyi hakama maman. Amma dayake sunsan yace yana dawowa zai taho ya tafi dasu sai suka ringa saka idon zuwansa kawai ba waya, Duk yan gari sunsan wannan karan ABDULAZIZ LIMBA na zuwa tafiya zaiyi da mamansa da Ummitansa dan haka aketa kewansu tin basu tafi ba. Ummitah karatunta yayi nisa hartana ss1 suna kokarin shiga ss2 amma babu labarin HAMMANTA, Tin suna saka ran zuwansa har suka cire rai suka ringa adduar idan ba wani abin ne ya samesaba. Ahankali rayuwa tafara sauya musu gatansu ya fara ragewa sbd duk abinda ya tanadar musu ya qare sun fara shiga damuwa da matsin rayuwa. Halinda suke ciki ba shine damuwa da quncinsu ba rashin jinsa da ganinsa dan haka suka sake dagewa da addua ba dare ba rana harma da azumi Allah kadai suke roqon ya saka yana lafiya Allah yasa wannan shirun nasarace tafe garesu. *******Babban tashin hankalin daya riski rayuwarsu shine bayyanar dangin mahaifinsu ABDULAZIZ din garin da babbar maganar data saka mama kusan somewa saida aka riqeta. Ummitah suke so a basu sbd sun samu labarin ABDULAZIZ yayi kudi zuwa ma zaiyi ya tafi dasu bazaa sake jin labarinsu ba dan haka basu Aminta da hakan ba Aure zasuwa Ummitah anan ta yanda bazai taba barin nan dinba har abada. Ba mama kadai ba ko inna tana gama jin zancen kuka ta fasa tana rokon ALLAH ya kawo musu ABDULAZIZ kafin a lalata rayuwar Ummitah da suka daukan masa alkawari da rayukansu akan bazasu taba barin rayuwarta ta lalaceba. Su kawu kuwa acikin kankanin lokaci suka bude wuta akan hakan wanda magana har a gaban me gari dayaqi yadda da maganarsu shima. Mama kuka ta zube a gabansu tana rokonsu akan kada suyi hakan su bari ABDULAZIZ ya dawo qasar. Kallanta kawu shehu yayi yanajin wani baqin ciki na taso masa sbd jin wato ma ABDULAZIZ din baya qasar sbd samun daukaka gasunan yaransu sun danqare a kauye basa komai sai aure aure suna tara yara da qananun shekaru. Tsokin baqin ciki kawu shehun ya sake yana kallan kawu isyaku da shima baqin cikin yake yace "Wlh bazamu jirasa ba tinda ba shine ubanmu ba,aure kuma wlh babu wanda ya isa ya hanamu yimata aure tinda duka sa'anninta gasunan anmusu aure harda haihuwa wasu ma Duk kunbi kun mayarda yarinya sakarta shiyasa zaizo ya dauketa yakai qasar turawa ta qarasa lalacewa ko? To idan shi yafi karfinmu baimasan damu ba to ita kafin tafi karfin namu zamu nuna matsayinmu kanta" Cikin kuka mama ta dago jajayen idanuwanta zatai magana kawu shehun ya katseta a kufule da cewa "Ke wlh babu abinda zamuji Ke wlh ma vazata qara sati a gida ba nan da kwana uku idan bata fidda miji ba aure zamu daura mata da 'dan uwanta 'dan wajen isyaku jibi a daura musu aure mu tafi da ita ta tare ai shikenan idan ya dawo ya ringa kai mata ziyara acan da duk ma abinda ze kai mata ya ringa kai mata acan" Hawaye masu tsananin zafi ne suka gangarowa mama sbd a bayyane tsananin kwadayi da baqin ciki da hassada ce zata sakasu yin abinda sukeson yi. Qara mama ta sakasu amma karshe sune aka bawa gaskia sbd sune dangin uba dan haka hankalin mama dana maigari ya tashi sbd bazasu taba bari a iya lalata rayuwar Ummitah ba sbd itace rayuwar ABDULAZIZ kuma kuzarinsa na nan duniya. #MAMUH #LIMBAS #BROTHERS LOVE ZAFAFA BIYAR KALBIM 500 mamuhgee A DUNIYATA 500 Huguma AJIYA A DUHU 500 Billyn Abdul KIRJIN ME HANKALI 500 Miss xoxo Pay at 0022419171 AccessBank Maryam sani gummi Shedan biya 09033181070 Or mtn vtu at 09032345899*_Arewabooks@Mamuhgee_* 13 *ZUZEAM VENTURES* Best APHRODISIAC 08144015291 Aslm barkanmu da wannan lokaci Ina Mai farin cikin sanar daku cewa Zuzeam ventures takawo maku ingantattun magunguna masu inganci cikin Aminci Muna da kaya kamar haka Mallaka Maganin sanyi Maganin cire tumbiMaganin farin jini Maganin matsiMaganin mata Maganin sa ni’ima da dandano Dulka Amare Set na gyran jiki Set na amarya Tabaje tsumin Gomba Xuma kiba ta hips and Brest Magungunan gyran Brest Magungunan Karin hips Maganin sliming Muna da kaya masu inganci cikin sauki da rahusa Ina wadda keneman mallaka sahihiya quaranty wlh hajiya kixo ga zuzeam ventures xakiji ddin mallaka duk fadin ran ogah duk fadansa wlh sai yyi sanyi 08144015291 Idan maganin mata kikeso akwai Idan gyran jiki kikeso gyran fata gyran Brest magungunan sa kiba da hips DOMIN samunta Kai tsaye kira wannan no 08144015291 DOMIN mgn da ita whatapp 08144015291muna tura kayanmu ko ina cikin iKon allah 🥰👌🏻 Bononza Bononza Tsimin mangoro 1k🥭 Tsimin dabino 1k Gumba ukku balai 700 Gumba aya da nonon rakumi 700 Garin kafi ciccibi 500 Garin bata gaban kishiya 500 Matsin mallaka tada zaune tsaye 2500 Turaren mallaka ba aba mai kishiya 2500 Total kayan 9500 Za a bakisu akan 3800 Kuma mutun goman farko nadakyautar Abun 2k 🗣️🗣️🗣️🗣️🗣️🗣️ ASSALAMU ALAIKUM ALHAMDULILLAH YAN UWA NEW PROMO YA KAMMALA💃🏽💃🏽💃🏽😁😁😁 da 5k dinki ki kwashi kayan 12k hajiyata 💃🏽💃🏽💃🏽😃🙃Kazar gadali ta mallara Rabi 3500 Tsimin gam gam 1500 Ruwan kara zunzurutun dadı😋800 Garin 7in1 1k Gumba 3 balai 500 Gumba kwakwa da dabino 500 Infection ruwan tsarki 1k Garin zunzurutun dadi 1200 Matsin ba a fira d wando 500 Matsin infection mai matse mace gam 500 12k All at 5k kedai dannan link dinnan don samun naki ki maza kiyi bucking koda kudinki saida Rabonki ************** Kwana biyu daga mama har Ummitah da inna babu me walwala cikin tsananin damuwa suke wanda ya saka inna fara ciwo ahankali dama ga tsufa sosai ya cimmata komai yi mata akeyi ko mama ko Ummitah. Maigari baba Alhassan ma duk yanda zai samu mafita ya nema babu dan haka ya kira Mama sukai shawara akan kudin dayake ganin shi kadaine mafita garesu dan hanawa su kawu shehu Ummitah. Shiru mama tayi sbd nauyi da girman zancen amma kuma basuda zabin daya wuce hakan sbd shi kansa ABDULAZIZ zaifi jin sassaucin hakan akan su bari a tafi da Ummitah dan haka ta sauke numfashi ta dago ta kallesa shima shiru yayi sbd SAYYID shine 'dansa tal namiji wanda yake so fiyeda duka yayansa dasuke mata kuma dika dika su hudu ne uku mata sai sayyid din wanda yake qaraminsu hakama duka duka baifi shekara goma sha takwas ba zuwa da sha tara so yake shima yayi karatu ya zama kamar ABDULAZIZ da suke kallo kaman wani taurari dayakeda haske mara dishewa,Amma ayau ya yadda ya dirqushe masa rayuwa ta hanyar daura masa aure da Ummitah dan hanawa dangin ubanta tafiya da ita. Mama ma ganin kaunar Baba alhassan din dayakewa ABDULAZIZ ya sakata amincewa take gashi Sayyid din ma yanada son koyan karatu shiyasa kullum yake yawo makarantar yan boko yana kallansu yanda suke karatu. Koda mama ta isa gida da maganar inna jikinta ya rikice wanda ciwon ajali kawai yazo mata ba bata lokaci ta zama wani iri haka suka kwana akanta anata abu daya asubar fari tace ga duniyar nan. Sabon damuwa da tashin hankalin rashin inna suka shiga itada Ummitah dan haka suka ringa kukansu su kadai. Rasuwar inna ta saka su kawu daga auren dan haka a kwana biyu Ummitah ta fita hayyacinta 'dan uwanta kawai take tsananin so da buqatan gani. Mama kuwa rashin inna dana ABDULAZIZ dinne ya ringa zuciyarta itama amma basu janye uzurinsu na aurenba dan haka inna na kwana bakwai da rasuwa aka saka Ummitah a lalle ba sanarwa sedai kawai aka ringa tayasu murnan dole. Kafin labari yakaiwa su kawu su taho tini baba alhassan yaje gurinsu ya nema aure da dan arzikin daya rage masa duka ya basu sbd zalama suka amince atake ma suka daura auren kafin yan neman auren su tafi. Mama kuwa duk abinda ya rage musu ta tattara ta siyar tai bikin Ummitan ta siya mata kayan daki da abubuwan buqata aka kaita. Acan gidan baba alhassan ma gyara musu daki daya yayi lafiyayye da bandaki aka gyarawa amarya ta tare. Ummitah tayi kuka kaman zata zarewa mamanta hakama maman tayi kuka hadda ciwo amma haka suka rabu. *****komai ya lafa ankwana biyu kuma Ummitah bata dena zuwa makaranta ba wadda karshe ma itada sayyadin din mijinta sika koma suna zuwa tare daga karshe ma aji daya aka yan dubaru aka sakasu sbd ta dan ringa koya masa abinda bai ganeba tinda ta dade a karatun ita. Bayan auren shakuwa da kusanci sosai ya shiga tsakanin Ummitah da sayyid suka fara son junansu sosai, Soyayya me karfin gaske sayyid yake mata kaman yanda itama take masa dan haka hankalin mama dana baba alhassan ya kwanta sukasake duqufa adduar dawowan ABDULAZIZ. Suna shiga ss3 Ummitah ta samu ciki wanda bayyanar rashin lafiya a tattare da ita ne ya saka aka san da cikin dan haka kulawan da ake bata ya qaru sosai. Sayyid kuwa dadi ya ringa ji dan baima damu da rashin tsayuwarsa a rayuwa ba sbd tsananin son dayakewa Ummitah da duk abinda ya shafeta. Bai taba ganin ABDULAZIZ ba amma kaunarsa yake mai tsafta da karfin gaske sbd irin tsananin son da Ummitah ke masa dan haka shima yake shirye daya bisa yayi masa biyayya har inda karfinsa ya qare. Ahankali ahankali ciwon laulayi ya koma ciwo a jikin Ummitah, Ga karatu wanda dole ta dena zuwa ga sanyi daya shigeta sosai kwata kwata cikin baizo da saukiba ko kadan dan haka mama taxo ta dawo da ita hannunta tana kulawa da ita. *******Rashin jinsu kwata kwata tsawon lokaci me tsayin gaske ya saka ya shiga damuwar data taba aikinsa wanda ya saka masa dawowa da abinda yake yi baya dan kuwa lalacewa komai yayi sbd damuwa dan haka dole komai aka dawo farko kuma ba damar tafiya sbd aikine da zai sauya rayuwarsa gaba daya idan yayi nasara dan haka dole ya dage ya tsaya wanda hakan ne ya haddasa masa daukan tswon lokaci meyawa na shekaru bai dawo ba. A cikin nasara da yardar Allah ya kammala tareda samun zuwa na daya wanda ya janyo masa wata irin suna da daukaka. Murna da farin cikin mutanensa dasu alh saad suka shiga anata celebrating tareda tayasa murna hakama kamfaninsa take ya samu shiga jerin kamfanin da aka dan san dasu. A lokacin ne babu bata lokaci ya tattara ya koma Italy daga can ko sati biyu baiyiba ya sauka Nigeria. Bai kwana a abuja ba ya isa garinsu sbd daukosu kawai yakeda niyar yi su dawo abuja. Lafiyayyan gida me kyau da tsari dan girma ya mallaka a abujan wanda babu abunda baa sakaba na jin dadin rayuwa wanda tin bai dawoba qasar aka gama komai na gidan da tsarinsa. Da rana kwatsam ya sauka a garin wanda motarsa ta saka jamaa taruwa a kofar gidansu mama. Ummitah dake zaune mama da sayyid na gefen suna kokarin ganin taci abinci da lemu da abarban data saka sayyid siyo mata sbd shima gaba daya ya haukace da nema sbd kulawa da ita da Buqatunta gashi kusan ya tare gidan maman shima sbd ita. Mama na dagowa ta kallesa saida gabanta yayi mummunan faduwa sbd gabaki daya baiyi kama da ABDULAZIZ dintaba Hawayene suka fara gangarowa daga idanuwanta masu tsananin zafi da batasan ma na menene ba. Ummitah kuwa qamshinsa daya cike tsakar gidan ta shaqa da kyau har cikin cikinta taji wani irin sanyi na mamaye zuciyarta zuwa gangar jikin. Itama hawaye ne suka fara gangarowa daga idanuwanta tana kasa dauke idanuwanta daga kansa duk da kuwa tsananin kwarjinin dayake dashi na cikar haiba. Sayyid hannuwansa biyu ya saka suna rawa yafara goge mata hawaye yana jiyowa yayiwa ABDULAZIZ din kallo daya ya sauke idanuwansa. Kwata kwata bai lura da cikin dayake jikinta ba sbd abine da bazai taba kawowa akansa ba koda kuwa mafarki fararen idanuwansa masu wani irin kyau ya zuba mata zuciyarsa na samun abincin datai shekaru bata samuba ya ware mata hannuwansa ahankali tareda ambatar sunanta da wani irin sautin daya sakata fasa kuka tana miqewa da karfin da sayyid baitaba sanin ayanzu tanada shi ba sbd rashin lafiya ta tinkaresa da gudun gaske ta fada jikinsa yai wata kyakkywar runguma yana rintes idanuwansa wani irin farin cikim dayafi komai na rayuwarsa na rufesa. Mintina sukai ahakan yana sauke ajiyan zuciya ita kuma tana kuka sosai tana kankamesa tana ambatar sunansa kaman zata bude masa zuciyarta yaga irin abinda takeji na kewansa datai da tsananin Buqatansa datake. Mama ma kuka takeyi sosai wanda ya sakasa sassauta riqon da yayiwa Ummitah jin wani wani irin tudu ya dan tokaresa. Bude idanuwansa yayi ahankali tareda zubawa mama yana kasa sakin Ummita wadda itama ta sake qanqamesa. Wani irin ciwon kai yaji ya sara masa a tsakiyar gefen kansa ya lumshe idanuwansa da suka dan sauya ya bude yana zare Ummitah a jikinsa ahankali. A gabansa ya tsayar da ita ya zubawa fuskanta datake sunkuye tana kuka ido yana mata kallan daya saba mata duk yazo na karantar meye ya sauya a tattare da ita. Tin daga fuskanta yaji zuciyarsa na nauyi yafara gangaro da idanuwansa har zuwa cikinta daya fito qarami dashi. Kaman cikin haihuwa yake gani a jikinta wanda yasan imaginations nasa kawai dan haka ya dago ya zubawa fuskanta ido yana son ta kallesa amma ta kasa dagowa sai kuka tasake sakarwa. Mama data kasa dagowa ya mayarwa da kallansa sai lokacin ya lura da sayyid daya taho ya tsaya gefensu yana kallansu cikeda kauna da burgewa tareda rashin son kukan Ummitah. Mama ce tayi karfin halin dagowa tanai masa sannu da zuwa share hawayenta ta nufi daki dauko masa tabarmarsa da haryanxu bata taba fiddawa wani ya hauba sbd dan shi suka siyeta. Tana saka kafarta daya daki kafin ta saka dayar ya kasa shiru da muryansa me nutsuwa da taushi yace "Mama meye wannan a jikin Ummitah?? Cak ta tsaya agurin batareda tayi gababa ko baya tana sauke numfashi da ajiyar xuciya me sanyi kafinta juyowa ahankali kai tsaye tana daukan matsayinta na uwa ba shakka tace "Juna biyu ne a jikinta ga mijinta nan a tsaye ku gaisa bara na dauko maka gurin zama" Tana fadar hakan ta qarasa wucewa ciki tana sauke ajiyar zuciya da numfashi sbd ba amfanin boye boye da tashin hankalin abinda ya riga ya faru ba sauyi kaddararsu taxo ahakan. Shiru gurin yayi wani irin mummunan nauyi kansa yayi da maganar tareda wani irin nauyin kirji daya kusa taba ganinsa dan haka tabarman data shimfida ya qarasa baya gani sosai ya zauna yana kasa kallan maman sai Ummitah da rayuwarta ta riga ta lalace dan haka take idanuwansa sauya zuwa wani irin jajir kaman an zuba musu borkono. Maganan bayan rabuwa da barka da zuwa mama ke masa amma kwata kwata baya jinta jinsa gava daya ya dauke iska kawai yake ji kaman yana kada masa hakama ganinsa yara rawa dan haka bai fahimci komai sosai ba saida Ummitah ta gama kukanta ta dago ta kallesa ta fahimci kwata kwata baya hayyacinsa ma kuma maganar aure da cikin ne yake neman zarar dashi kuma tasani babu abinda zai hanasa raba auren dan haka cikin sanyin murya ta bude baki tace "HAMMA inasonsa zanci gaba da zama dashi" Rintse idanuwansa da suka kusa watse masa yakeji yayi da qarfi wani nauyin gaske na danne kirjinsa. Sayyid daya shiga damuwa da tsoro numfashi ya sauke me sanyi yana kallan Ummitah da shi gava daya ganin ABDULAZIZ din ya tsinkar dashi. Mama ma numfashi me sanyi ta sauke sbd a baya kam daya dawo da wuri yace zai raba auren bazata hanaba amma yanxu ga rabo ansamu kuma ace zaa raba auren bame yiyuwa bane. Mama ce ta karbi zancen kai tsaye da cewa "Sayyid yaron kirki ne kuma yana kaunar matarsa da abinda yake cikinta dan haka ba abin damuwa bane ga abinda Allah ya kaddaro, A matsayina na uwa gareku ina umartanka da kada kace komai ka karbi hukuncin Allah da hannu biyu" Bude idanuwansa yayi suna sake sauyawa kirjinsa na wani irin radadi me ciwon gaske sbd mata uku dayake so fiyeda komai a rayuwarsa da komai daya mallaka ga biyu a gabansa daya tace tana sonsa daya tace bata aminta yace komaiba. Jin yayi zuciyarsa na neman bugawa dan haka ya sauke wani irin numfashi me zafin gaske ya dago ahankali ya zubawa sayyid idanuwansa sai yaji zuciyarsa ta sassauto sbd basan tayaya zaiqi abinda Ummitah ta bude baki ba tace tanaso. Zaunawa sayyid din yayi suka gaisa Nan mama da Ummitah suka fara yi masa gaisuwan nutsuwa da fada masa damuwar rashin ganinsa. Baida nutsuwa da walwalan fira dasu sosai sbd abinda ya tadda din dan haka ba maganar tafiya ranar dole a haka koma sai washe gari ya dawo inda baba alhassan da mama suka sanar dashi komai na abinda ya faru. Numfashi kadai ya sauke tareda yi musu godia baice komai akan dangin mahaifinsa ba ya sanar dasu tafiyarsu. #MAMUH ##ZADEEN'S ##LIMBAS ZAFAFA BIYAR KALBIM 500 mamuhgee A DUNIYATA 500 Huguma AJIYA A DUHU 500 Billyn Abdul KIRJIN ME HANKALI 500 Miss xoxo Pay at 0022419171 AccessBank Maryam sani gummi Shedan biya 09033181070 Or mtn vtu at 09032345899*_Arewabooks@Mamuhgee_* 14 *ZUZEAM VENTURES* Best APHRODISIAC 08144015291 Aslm barkanmu da wannan lokaci Ina Mai farin cikin sanar daku cewa Zuzeam ventures takawo maku ingantattun magunguna masu inganci cikin Aminci Muna da kaya kamar haka Mallaka Maganin sanyi Maganin cire tumbiMaganin farin jini Maganin matsiMaganin mata Maganin sa ni’ima da dandano Dulka Amare Set na gyran jiki Set na amarya Tabaje tsumin Gomba Xuma kiba ta hips and Brest Magungunan gyran Brest Magungunan Karin hips Maganin sliming Muna da kaya masu inganci cikin sauki da rahusa Ina wadda keneman mallaka sahihiya quaranty wlh hajiya kixo ga zuzeam ventures xakiji ddin mallaka duk fadin ran ogah duk fadansa wlh sai yyi sanyi 08144015291 Idan maganin mata kikeso akwai Idan gyran jiki kikeso gyran fata gyran Brest magungunan sa kiba da hips DOMIN samunta Kai tsaye kira wannan no 08144015291 DOMIN mgn da ita whatapp 08144015291muna tura kayanmu ko ina cikin iKon allah 🥰👌🏻 Bononza Bononza Tsimin mangoro 1k🥭 Tsimin dabino 1k Gumba ukku balai 700 Gumba aya da nonon rakumi 700 Garin kafi ciccibi 500 Garin bata gaban kishiya 500 Matsin mallaka tada zaune tsaye 2500 Turaren mallaka ba aba mai kishiya 2500 Total kayan 9500 Za a bakisu akan 3800 Kuma mutun goman farko nadakyautar Abun 2k 🗣️🗣️🗣️🗣️🗣️🗣️ ASSALAMU ALAIKUM ALHAMDULILLAH YAN UWA NEW PROMO YA KAMMALA💃🏽💃🏽💃🏽😁😁😁 da 5k dinki ki kwashi kayan 12k hajiyata 💃🏽💃🏽💃🏽😃🙃Kazar gadali ta mallara Rabi 3500 Tsimin gam gam 1500 Ruwan kara zunzurutun dadı😋800 Garin 7in1 1k Gumba 3 balai 500 Gumba kwakwa da dabino 500 Infection ruwan tsarki 1k Garin zunzurutun dadi 1200 Matsin ba a fira d wando 500 Matsin infection mai matse mace gam 500 12k All at 5k kedai dannan link dinnan don samun naki ki maza kiyi bucking koda kudinki saida Rabonki *********** Washe gari yana zuwa baba alhassan baiyi musu ba akan tafiya da zaayi harda sayyid sbd shi hakanma yai masa dan haka babu bata lokaci aka fara shirye shiyen tafiya sai kuma daga baya baba alhassan da mama suka roqesa akan yabari su Ummitan da sayyid su gama exams dinsu da aka fara ta waec. Bai yadda ba amma hakanan mama ta tirsasa ya amince dan haka aka sake haukata kauyen gaba daya da abubuwan alkhairi sbd hatta gidan baba alhassan saida akai masa sauye sauye hakama ya bawa baba alhassan din kwangilar gina masallaci da rijiya Allah yakaiwa inna da iyayensa ladan. Akan dole ya koma abuja kafin su gama exam din sedai yana zuwa ko kwana biyar baiba ya sake dagawa zuwa lagos daga canma wata tafiyar yayi. Su kuwa su mama renan cikin suka ci gaba dayi dan daman sun boye masa ciwo dataketa fama dashi akan cikin sbd a samu yabarta ta kammala exams din sbd shi a nasa so yayi idan sun tafi saita haihu saitayi exams dinta aguri me kyau har ita har Sayyid din wanda ya dage sosai sbd so yake ya zama me ilimin da shima zai bata kulawa kaman Hamman. Yanayinta da yanda ciwo yaketa gaba ya saka baba alhassan ya daukesu sukaje capital a wani asibiti me kyau akai mata register na awo dan ta ringa zuwa akai akai kuma har lokacin basu sanar da ABDULAZIZ ba sbd kada su saka masa damuwa gashi baya ma kasar. ************ A bangaren ZAADENs kuwa suma komai na tafiya daidai tinda suka samu farin cikin rayuwarsu hasken idaniyarsu, JANNAH ZAADEN wadda wani lokacin suke kira na JAN ta taso cikin rayuwar kulawa da wani irin gata da asalin hutu da tarin arzikin da koyaushe yake qaruwa a familyn, Basusan menene rashi ba kwata kwata sai na iyaye da kanni da suka rasa sai kuwa asalin farin cikinsu dayar sanyin idaniyarsu wato zayneb wadda a yanzu Jan ce ta maye musu gurbin nata, Babu abinda suka sani a rayuwa bayan samu da hutu tareda jin dadi da kwanciyar hankali sai zurfafa ilimi da yawon qasashe. Tsananin son da Ammar yakewa Jannah kusan har mamaki yake bawa Mimi sedai duba da Mum dinsa ce sai ta dena mamaki. A familyn zaadens babu wanda ba rayuwar class da wayewa tareda tsatsan kudi yakeyiba, Kyawawane suma kusan suma duk kamanninsu daya hakama kana ganinsu zakace familyn black Americans ne musamman Ammar dayafi su haske sbd mum dinsa nada haske fiyeda su Dzad. Jan nada shekara 9 a school school dinta suka fara noticing kwata kwata batason duk wank physical activities da farko suna mata dubarun ta ringa yi amma sam bataso da suka dam takura saisuka lura tana farawa take fara zufa harma da shortness of breath. Dayake school din masu kudi ne sosai sam basa zaqewa akan komai na student saida izinin iyayensu dan haka suka sanar da iyayenta akan a lura da hakan kokuma akaita checkup. Dayake Mimi sukai magana da ita sai bata wani dauka serious ba dan haka bata fadawa su Dad ba tinda ba wani zama yake ba sukuma yayun nata sunata fama da karatunsu. Kasancewan Jan din ta taso cikin yayunta maza sai iyayenta da masu aiki sai batada wani rawan kai ko hayaniya gata yayi mugun mata yawa dan haka take da wani irin class tin tana yarinya sam bata son mutane sosai itama sedai zuciyarta nada wani irin sanyi da tausayi tareda rashin karfin hali kawai dai batason shiga mutane ne sbd bata sabu dasu ba a cikin gidansu ne kadai take sakewa tayi wasa da tsalle a cikin yayunta datake tsananin so itama. A karo na biyu school suka sake yiwa Mimi maganar yanayin jannah din amma still tace zata sanar da yayunta ko dad dinta sukace to. Da jannah din ta dawo school kallanta Mimin tayi taganta healthy da ita dan haka sai ta sake tinanin sunason fara takurawa yara ne school din dan haka ta share zancen. A makaranta sunga sam jannah din babu wani sauyi hakama iyayen sunqi cewa komai sai kawai suka kyale aka dena tirsasata duk wani physical activity sai kuwa hakan yayi mata dadi ta dena damuwa ta sakewarta da friends nata. A haka karatunta yafara nisa tafara zama yan mata kwatsam ranar da sukai family dinner na murnan gama karatun mahir zadeen kwata kwata ya zama cikakken chairman na ZADEENS GRP sunata murna cikin nutsuwa da kwanciyar hankali irin na masu kudin da babu hayaniya. Ammar ne ya iso da daddaren sbd flight da bai samu ba daga italy daya tafi dan haka koda ya iso dukkaninsu suna open dinner a dayan lafiyayyan dining dinsu dake kusa da swimming pool na gidan qamshin ruwan me tsafta dana flowers dake zagaye da gurin yana tashi ahankali hakama ga iska me sanyi da nutsuwa yana kadawa ga haske koina dake gurin. Isowansa ya saka Jannah tasowa da w Gudun gaske ta tinkaresa shima cikin farin ciki da kaunar dayake mata wadda sam batada sirki ya bude hannayensa ta qaro gudun gaske. Tana gap da isa gurinsa kirjinta ya kasa daukan stress da rapid breathing din take tsaya cak idanuwanta suka juye ta yanke jiki a gurin ta zube. Ammar dinne ya ambaci sunanta da sauri yana qarasowa da sauri kanta cikin matsananin tashin hankali da mamaki. Juyowa kowa yayi yai jin yanda ya ambaci sunanta suka ganta zube a qasa kaman ba rai a jikinta. Idan akwai abinda ya taba saka zuciyoyinsu tsayawa cak suna dauke wuta to wannan mugun ganin ne musamman Dad din dayaji jininsa na neman hayewa take kasa motsawa yayi. Maheer da saleem ne da Mimi suka taso da sauri sunayi kanta wanda tini Ammar ya daukota gaba daya yana kiran sunanta idanuwansa na qanqancewa. Da karfin gaske yace a kira doctors bama doctor daya ba, Saleem ne yayi saurin dawowa ya dauki wayarsa yana budewa yafara neman likitoci maheer kuwa bayan Ammar din yabi shima yana fidda wayarsa dan kiran wata asibitin. Mimi ma bayansu tabi dad ma sai alokacin yaji wani mugun karfi ya zuwar masa ya miqe yabi bayansu shima yana kokarin daidaita wayarsa a hannunsa dan kiran wani likitan. Sama sukai inda dakin jannah din yake sedai ko isa basuyiba suka juyo sbd maheer daya dauko keys na mota sbd ganin bazasu iya tsayawa isowan likitocin da suka kira ba. Kusan keys hudu ne a guri daya ya kwaso su a palo ya watsar da sauran akan sofa suka nufi kofa har lokacin tana hannun Ammar wanda yake jin kaman zai zare sbd ganin zufan datake tsananin yi bakinta na bushewa kaman wani abin sihiri. Dad ne ya budewa Ammar kofan motar ya shiga da ita kafin shi ya shiga Mahir yaja suka bar gidan da wani irin speed. Saleem ne ya fiddo wata motar yabi bayansu suka Mimi gida tareda masu aiki da suketa mata sannu da fatan Ba wani abin ne yake damun Jannah dinba. A hanyar zuwa asibitin maheer ne kadai idanuwansa ba akan Jannah din yake ba sbd yana drivin ne amma Ammar da Dad shiru sukai kowannensu ya zubawa fuskanta idanuwansu da suka sauya. Ammar yanada trauma da bata warke ba tin ta rasuwar Mum dinsa a duk lokacinda yaga wani a kwance kamar ba rai a jikinsa sai kansa yayi kaman zai juye sbd tinda aka haifesa mum dinsa take kwance cikin ciwo harya girma ta rasu a kwance take dan haka abin ya taba kansa sosai duk da Allah ya taimaka an samu ya dawo daidai amma haryanxu wannan trauma din tana cikinsa, Ganin jannah a wannan yanayin yanzu ya sakasa kansa neman zarewa dan haka hannunwansa suka fara rawa ahankali ahankali wanda ya saka Maheer fahimta duk da yana tuqi ya dan juyo ya kalli Ammar din ya kalli dad yace "Dad, Ammar" Ammar din dad ya kalla cikin karantar yanayinsa ya miqa hannunsa ya kama nasa tareda dan damqewa. Dago idanuwansa da suke sauyawa yayi ya kalli Dad din cikin sanyi da kokarin hana hannuwansa dake rawa rawan. Kallan kwantar da hankali dad din yayi masa yana kasa cewa komai sbd shima kwarin gwiwan yake nema a basa sbd ya yadda ya rasa fiyeda rabin dukiyarsa akan Jannah tayi ko ciwon kai ne amma Ammar ma wani bangaren ne na rayuwarsa dayakewa wani irin kauna wadda take ta kasancewansa jinin zayneb data bar musu a duniya dan haka yake jinsa a ransa sosai. Suna isa asibitin a cikin gaggawa aka karbeta akai ciki da ita doctors din da duk suka kira suna bin dakin da aka shige da ita suna shigewa. Su kuwa tsayawa sukai batareda kowannensu ya zauna ba se dad din kawai sbd shi kam yana buqatan zaunawan sbd bp dinsa dayaki ba daidaiba. Saleem na isowa Ammar da maheer dake tsaye ya kalla kafin yayi gurin dad ya zauna kusa dashi yana cewa "Dad you're not looking good kana buqatan ganin likita kaima" Girgiza kai dad din yayi yana bude baki a hankali yace "No Am ok" "But dad.... "Saleem i said am fine,ok? Kasa yadda da hakan saleem yayi amma ya kyalesa kafin suki Jannah din tukuna. Maheer wayoyi yafara yi da wasu kwararrin likitocin guda biyu dake india yana fada musu abinda ya samu Jannah din shi kuwa Ammar kofar dakin ya zubawa idanuwansa baya kyaftawa kansa na juyawa sbd a irin haka ne da hannunsa ya dauko mum dinsa ya kawota asibiti sedai aka fito kaman haka akace masa ta rasu dan haka ya kasa motsawa daga inda yake kofar dakin kawai yake kallo. Duk dubaru da abinda doctors ke tinani dan ta farfado baiyiba numfashinta da bugun zuciyarta ya dakata wanda ya sakasu shiga fargaba da shakkar abinda suka fara tinani dan haka cikin gaggawa aka fara bincike da Awo awo. A cikin qanqanin lokaci jannah ta koma kaman wadda ta jima tana jinya bakinta ya bushe ya sauya hakama tayi wani irin pale gashi bata farfado ba. Sai zuwa asuba aka bari suka shiga inda take bayan sunyo sallah sun dawo kenan. Suna shigowa kowannensu shiru yayi suna kallanta cikeda fargaba da mamakin sauyinta na lokaci daya. Saleem ne kadai ya iya kiran sunan Allah yana qarasa gurinta da sauri sedai ba ikon tabata dan oxygen ne ma a hancinta. Dad kuwa likitocin dake tsaye ya kalla cikin sanyi na nutsuwa yana cewa "Dr Abraham wats wro... Katsesa Dr Abraham yayi da cewa "She'll be fine Sir We're waiting for her results so lets all wait... Magana saleem zaiyi dad ya katsasa da cewa "Yace ba wani abu babba bane so mu jira din" Guraren 8 na safe Mimi ta iso asibitin batareda da breakfast ba sbd tasan babu wanda a cikinsu zai iya cin abinci a asibiti sbd sunada qyanqyami duk da asibitin kyanta ma kusan kaman a hotel yake. #MAMUH #ZADEENS #LIMBAS #BESTYSTORY ZAFAFA BIYAR KALBIM 500 mamuhgee A DUNIYATA 500 Huguma AJIYA A DUHU 500 Billyn Abdul KIRJIN ME HANKALI 500 Miss xoxo Pay at 0022419171 AccessBank Maryam sani gummi Shedan biya 09033181070 Or mtn vtu at 09032345899*_Arewabooks@Mamuhgee_* 15 *ZUZEAM VENTURES* Best APHRODISIAC 08144015291 Aslm barkanmu da wannan lokaci Ina Mai farin cikin sanar daku cewa Zuzeam ventures takawo maku ingantattun magunguna masu inganci cikin Aminci Muna da kaya kamar haka Mallaka Maganin sanyi Maganin cire tumbiMaganin farin jini Maganin matsiMaganin mata Maganin sa ni’ima da dandano Dulka Amare Set na gyran jiki Set na amarya Tabaje tsumin Gomba Xuma kiba ta hips and Brest Magungunan gyran Brest Magungunan Karin hips Maganin sliming Muna da kaya masu inganci cikin sauki da rahusa Ina wadda keneman mallaka sahihiya quaranty wlh hajiya kixo ga zuzeam ventures xakiji ddin mallaka duk fadin ran ogah duk fadansa wlh sai yyi sanyi 08144015291 Idan maganin mata kikeso akwai Idan gyran jiki kikeso gyran fata gyran Brest magungunan sa kiba da hips DOMIN samunta Kai tsaye kira wannan no 08144015291 DOMIN mgn da ita whatapp 08144015291muna tura kayanmu ko ina cikin iKon allah 🥰👌🏻 Bononza Bononza Tsimin mangoro 1k🥭 Tsimin dabino 1k Gumba ukku balai 700 Gumba aya da nonon rakumi 700 Garin kafi ciccibi 500 Garin bata gaban kishiya 500 Matsin mallaka tada zaune tsaye 2500 Turaren mallaka ba aba mai kishiya 2500 Total kayan 9500 Za a bakisu akan 3800 Kuma mutun goman farko nadakyautar Abun 2k 🗣️🗣️🗣️🗣️🗣️🗣️ ASSALAMU ALAIKUM ALHAMDULILLAH YAN UWA NEW PROMO YA KAMMALA💃🏽💃🏽💃🏽😁😁😁 da 5k dinki ki kwashi kayan 12k hajiyata 💃🏽💃🏽💃🏽😃🙃Kazar gadali ta mallara Rabi 3500 Tsimin gam gam 1500 Ruwan kara zunzurutun dadı😋800 Garin 7in1 1k Gumba 3 balai 500 Gumba kwakwa da dabino 500 Infection ruwan tsarki 1k Garin zunzurutun dadi 1200 Matsin ba a fira d wando 500 Matsin infection mai matse mace gam 500 12k All at 5k kedai dannan link dinnan don samun naki ki maza kiyi bucking koda kudinki saida Rabonki ************** A tashin farko da likitocin suka fara samun results nata abinda suka samu shine ya sakasu haduwa meeting a tsakaninsu sbd tabbatarwa. Cardiomyopathy wanda yake leading to heart failure ne wanda suka tabbatar suka sake kwanaki suna tabbatarwa kafin suka yanke shawarar sanar da ZAADENs din wainda a cikin kwanakin suna cikin matsanancin halin damuwa da quncin da basu taba sanin dashi ba, Dukkaninsu sun jingine ayyukansu sai sintirin asibitin sukeyi gashi har lokacin bata farfado ba ta koma wata kalar tausayi tayi fari fat da ita gata yarinya shiyasa tausayinta yake qara rikita zukantasu. Mimi ce da Maheer a cikinsu suka fisu karfin hali dan kuwa dad dai yana gida yana karban treatment na kwantar da hankali da damuwa da akeson ya cire a ransa. Doctors buqatan ganin Dzad din da kansa sukai sbd tattaunawa dashi da familynsa. Dzad din tareda Maheer da Mimi suka iso asibitin sbd Ammar da saleem suna asibitin tinda safe. Koda suka iso Maheer ne ya fara shigowa dakin da jannah din take sanye cikin black giorgio Armani Suits Tukuna Dzad Sanye cikin Armanis din shima amma masu kauri wata tsadaddiyar Cardigan Mimi na gefensa cikin doguwar luxury abaya ash. Saleem dayake tsaye yana waya sanye cikin sweatset na balenciaga ash juyowa yayi yana qarasa gurin Mimi ya dan rungumeta cikin kunnenta ya rada mata "Goodmorning Mimi" sbd bai kammala wayar dayake ba. Dad ma a cikin sauti kadan yace "goodmorning dad" Amsawa dzad din yayi yana maida kallansa kan Ammar daya taso ya qaraso gabansa ya rungumesa yana cewa "Komai zai zama daidai Ammar okay" Numfashi me sanyi da nutsuwa Ammar din ya sake yana cewa "Yes Dad insha Allah" Mimi ya kalla ta miqa masa hannu ya kama ahankali yana cewa "Goodmorning Mimi" "Meyasa kake wasa da naka health din Ko abincin kirki ka dena ci, I don't like seeing you like this My boy" Hannuwansa biyu ya zuba a aljihun Off-white burberries din dake jikinsa yana murmushin karfin halin kaunar Mimin nasa. Dukkaninsu akan Jannah suka maida kallansu Maheer na fidda wayarsa ya sanar da babban doctor din zuwansu. A office dinsa ya gayyacesu suka nufi office din dukansu banda saleem da aka bari a dakin yana waya. Zaunawa sukai dukkaninsu a office din banda Maheer dayake tsaye a bayan Dad Ammar da Mimi kuwa a kusa da juna suka zauna tana riqe da hannunsa cikeda kauna da kulawa sbd batason ganinsa cikin damuwa ko kadan. Dr Abraham kallansu yayi daya bayan daya kafin ya kalli dr Josh dayake gefensa yace ya gabatar da takardun dayake dauke da bayanin komai. Ajiye takardun na results dinta da suka gama sakawa a komai nata dayake computer ya koma ya zauna tareda kunna juyo musu da kan Computer din da zasu ga abinda zasu nuna musu yanda ya kamata. Dr Abraham ne ya kalli Dzad a natse cikin kwanciyar hankalin yanda zasu fahimcesa yafara zantukan da duka basa wani ganewa yana kwana da zancen sbd rage musu shock din zancen tukuna daga karshe yace, "Ms Jannah is suffering from Cardiomyopathy..... Shiru office din yayi babu wanda yace komai sai kallan kallo da sukewa doctor Abraham din da dr josh. Maheer ne ya bude baki cikin gaskiyarsa yace "And wat does that mean Doctors??? Numfashi Doctors din suka sauke a tare suna kallan familyn daya bayan daya dan ganin ko akwai wanda ya gane abinda suke nufi amma babu alamar sun ganen dan haka ya miqe tsaye ya zagayo gurin Dzad ya kallesa cikin nutsuwan datafi da baya kafin ya dawo da kallansa kan Maheer da yayi tambayar yace "Heart diseases,her heart is failing" Shiru dakin ya sake dauka babu wanda ya matso sai daya bayan daya suka fara dawowa suna kallansa dan tabbatar da abinda sukaji da kuma tabbatarda shin hakan ya fada kokuwa. Shima kallansu ya ringa yi daya bayan daya yana gyada kai with seriousness sbd su san bafa fada kawai yake ba he's morethan serious. Dzad ne yafara bude baki yace "Her heart is failing???? Yes Mr Zad and I'm sorry she's not in her first stage shes.... Yanke jikin da Dzad din yayi a gurin ya katse Dr Abraham din ya kallesa da sauri cikin tashin hankali Dr josh kuwa cikin sauri ya danna bell din kiran nurses dinsu yana tasowa shima. Mimi da Ammar kuwa mutuwar Zaune sukai a tare kowannensu jikinsa na neman qanqarewa da tashin hankalin da baa saka masa rana ba. Maheer kuwa cikin tashin hankali dayake cakar masa da kai ya rasa ma me zaiyi ya ringa kokarin daukan Dad din yana ambatar sunansa da karfi tareda neman taimakon gaggawa. Cikin gaggawa da sauri aka dauki dad din kaman ransa ya fice akai emergency dashi. Ammar silalewa yayi hannuwansa da kafafunsa na rawa ya zame qasa yana son numfashi me qarfi amma kirjinsa ya toshe ya tsaya cak wani abu me nauyin gaske ya danne masa kirji zuwa maqoshinsa. Idanuwansa wani irin ja sukeyi suna kasa hada hawayen kansu, Mimi ma hawaye tafara sosai tana kasa riqe kukanta tana cewa "Jannah dan Allah karki barmu kema,kece madadin zayneb Allah ya kawo mana dauki,innalillahi, Jannah meya hadaki da Cutar zuciya kema?" Saleem koda ya iso babbar masifar datafi komai a garesu ta fadowa familynsa dan haka shima shock din daya sakasa kasa yadda da zancen yayi ya sake tsare dr Abraham wanda ya zauna dasu ya sake musu bayani da karatun yanda ciwon yake dallah dallah tareda basu tabbacin yanzu tafara irin wannan ciwon na idan har ta zama exhausted ko wani physical activity da zai saka bugun zuciyarsa qaruwa to idan tayi collapsing zata ringa daukan kwanaki kafin ta farfado hakama Ahankali zuciyar zata cigaba da gazawa saga bugawa yanda ya kamata da blockage. Rawa jikik Ammar yakeyi sosai hakama Dukkaninsu daqyar ya iya bude baki muryansa na shaqewa da Tashin hankalin daya manta yaya yake a rayuwarsa ko gani sosai bayayi yace "Menene Mafitar ciwon da lafiyarta?? "Tanada sauran time na shekaru qalilan kafin Heart din yayi failing gaba daya...." "Wat are your suggestions then??? Maheer ya katsesa kai tsaye idanuwansa jajir kaman zai shaqe dr Abraham din ya rabasa da tasa zuciyar sbd wannan mugun labarin dayafi mutuwa daya basu. "Heart transplant" ya fada shima kai tsaye yana kallansu daya bayan daya yana kallan yanda zasu karbi zancen. Dukkaninsu da sauri suka dago suka kallesa cikeda mamaki me tsananin gaske da sabon shock. Shiru sukai dukkaninsu sbd tabbas Sun sake dawowa inda suka bari rayuwa tayo Uturn dasu a lokaci me tsanani da quncin da suka bari a baya akan Zayneb. Babu wanda ya sake cewa komai sbd tashin hankalinsu daya nunku tareda tsananin mutuwar jiki me ciwo da radadin zuciya. Gurin Dad dukkaninsu da aka hade daki daya da Jannah dan saukaka musu komai sbd dukansu suna son ganinsu guri daya. Wani irin kuka me tsima zuciya da saddakarwa Mimi takeyi a jikin Saleem wanda shima kukan yakeyi sosai yana shesheka. maheer wani irin ja idanuwansa sukai da fuskansa gaba daya ya zauna ya riqe kansa dayake jin kaman zai tarwatse sbd tsananin ciwo. Ammar kuwa ficewa yayi daga asibitin ya nufi gurin therapist dinsa sbd jin yake kansa na juyawan dayake neman rabuwa da wuyansa hakama ruwa kawai yake nema ya fada ko zai rabu da ransa ya huta da abinda yake ji. Allah kadai ya kaisa gidan Dr shilah lafiya sedai koda ya isa ko gani bayayi sosai hakama hancinsa har habon jini yake. Tana bude gidan ta gansa da sauri ta kwalawa masu aikinta kira suka taho suka kama mata shi kai tsaye toilet din office dinta suka nufa dashi tayi sauri ta kunna ruwa suka cika bathtub suka sakasa ciki banda kansa data riqe tana cewa ai sauri a kawo mata first aid. Wuni daya gaba daya zaadens sun koma kalar tausayi ga dad din ma tunda ya farfado aka sake nasa bayanin komai ya sake rikicewa daqyar akai controlling bp dinsa wanda shikenan idan ba Allah ya tsare ba ya kamu da hawan jini kenan. Ammar ma saida Mimi taje gidan dr shilah a daren ta taho dashi ya dan samu dawowa hayyacinsa dan haka suna dawowa gida ita taita kulawa dashi, A daren babu wanda ya rintsa a kaf familyn sbd suna cikin jarabawar Allah, Maheer ne a tsaye akan kowa yana kulaw sbd kowa yayi breaking suna neman shiga mummunan halin da duniya zata sani. Cikin ikon Allah washe dari guraren 9 na safe Jannah ta farka. Asibitin suka dunguma suka nufa kowannensu na kokarin boye damuwarsa sedai kana kallansu zakasan suna cikin qunci da damuwa. Cikeda kulawa da kauna suka ringa mata sannu Mimi kuwa zaunawa tayi kusa da ita tareda rungumeta ahankali tana shafa fuskanta cikeda kauna da kulawa jiki a mace. Shi kansa dzad ganin ta farfado ya sakasa samun karfin kuzarin warkewa. Bayani dr Abraham yayi musu na babu matsalar komai yanzu kawai dai abinda ya fada musu ne su kiyaye she should not be bothered with any physical activities ko exhaust and duk abinda zai kawo mata gudun bugawan zuciya a gujesa if not Heart din zata tsananta gudun failing wanda ba lallai tayi shekarun dayace mus din zatai ba. Motoci uku ne suka daukosu a jere zuwa gida Inda kaf masu aikin gidan suke tsaye suna jiran isowansu cikeda jimami da tausayin Jannah wadda suma masu aiki suke tsananin kauna sbd kwata kwata bata wani damu da matsayinsu ba tana kaunarsu da son sakewa a cikinsu. Koda motocinsu sukai parking a harabar gidan dake dauke da securities bude musu mota akai ana musu barka da zuwa musamman Dzad da kaman zaa zube qasa a durqusa masa. Jannah na gefen Ammar da Mimi tana tafiya a hankali cikin sanyi sbd karfin jikinta bai gama dawowa ba shes weak hakama tayi wani dan fayau da ita fararen idanuwanta ne kadai masu wani irin kyau ke amsa gaisuwa da sannun da masu aiki da Nannys dinta ke mata wainda tin tana yarinya suke kuma koda ta girma tace kar a sallamesu ta saba dasu. Nan Ama ce ta qaraso ahankali ta kamata daga gurin Ammar din wanda yake jin sanyi na mamayesa da nutsuwar datake ta dan lokaci sbd ganin sun dawo gida da jannah. #MAMUH #BESTLOVE #ROMANCE #LOVE #AY LIMBA #ZADEENS ZAFAFA BIYAR KALBIM 500 mamuhgee A DUNIYATA 500 Huguma AJIYA A DUHU 500 Billyn Abdul KIRJIN ME HANKALI 500 Miss xoxo Pay at 0022419171 AccessBank Maryam sani gummi Shedan biya 09033181070 Or mtn vtu at 09032345899*_Arewabooks@Mamuhgee_* 16 *ZUZEAM VENTURES* Best APHRODISIAC 08144015291 Aslm barkanmu da wannan lokaci Ina Mai farin cikin sanar daku cewa Zuzeam ventures takawo maku ingantattun magunguna masu inganci cikin Aminci Muna da kaya kamar haka Mallaka Maganin sanyi Maganin cire tumbiMaganin farin jini Maganin matsiMaganin mata Maganin sa ni’ima da dandano Dulka Amare Set na gyran jiki Set na amarya Tabaje tsumin Gomba Xuma kiba ta hips and Brest Magungunan gyran Brest Magungunan Karin hips Maganin sliming Muna da kaya masu inganci cikin sauki da rahusa Ina wadda keneman mallaka sahihiya quaranty wlh hajiya kixo ga zuzeam ventures xakiji ddin mallaka duk fadin ran ogah duk fadansa wlh sai yyi sanyi 08144015291 Idan maganin mata kikeso akwai Idan gyran jiki kikeso gyran fata gyran Brest magungunan sa kiba da hips DOMIN samunta Kai tsaye kira wannan no 08144015291 DOMIN mgn da ita whatapp 08144015291muna tura kayanmu ko ina cikin iKon allah 🥰👌🏻 Bononza Bononza Tsimin mangoro 1k🥭 Tsimin dabino 1k Gumba ukku balai 700 Gumba aya da nonon rakumi 700 Garin kafi ciccibi 500 Garin bata gaban kishiya 500 Matsin mallaka tada zaune tsaye 2500 Turaren mallaka ba aba mai kishiya 2500 Total kayan 9500 Za a bakisu akan 3800 Kuma mutun goman farko nadakyautar Abun 2k 🗣️🗣️🗣️🗣️🗣️🗣️ ASSALAMU ALAIKUM ALHAMDULILLAH YAN UWA NEW PROMO YA KAMMALA💃🏽💃🏽💃🏽😁😁😁 da 5k dinki ki kwashi kayan 12k hajiyata 💃🏽💃🏽💃🏽😃🙃Kazar gadali ta mallara Rabi 3500 Tsimin gam gam 1500 Ruwan kara zunzurutun dadı😋800 Garin 7in1 1k Gumba 3 balai 500 Gumba kwakwa da dabino 500 Infection ruwan tsarki 1k Garin zunzurutun dadi 1200 Matsin ba a fira d wando 500 Matsin infection mai matse mace gam 500 12k All at 5k kedai dannan link dinnan don samun naki ki maza kiyi bucking koda kudinki saida Rabonki ************ Kai tsaye Bedroom dinta Nan Ama ta nufa ita daman kuma babu ranar da baa gyara komai na dakin kaman yanda aka saba. Su kuwa sauran Yan gidan kowa Bedroom dinsa ya nufa sbd su samu kawunansu su sake su dan yi baccin da sukai kwanaki babu dan haka gidan yayi tsit masu aiki sukai suka kammala aikinsu na ciki suka tattara suka koma kitchen ba hayaniya. Acan Bedroom dinta kuwa toilet ta nufa ta tube ta shiga ruwan zafi dan gasa jikinta dayayi mata nauyin kwanciyar kwanaki. Ta jima a toilet din kafin ta fito daure da brown towel babba kanta na tsiyayar ruwan data wankesa sbd kwana biyun ba gyara duk ya dameta. Ko data fito Tea da snacks kusan kala hudu ne aka shigo dasu aka ajiye akan lafiyayyar table dake tsakiyar makeken Bedroom din nata. Ac ta dauki remote ta kashe gaba daya tana zaunawa tareda kunna hand dryer dake gefen dresser dinta tana son busar da kanta amma sai taji tanajin gajiya sosai irin wadda bata saba ji ba dan haka ta ajiye ahankali tareda danna bell dake gefen gadonta na kiran Nan. Ba bata lokaci akai knocking dakin tareda shigowa ta juyo kadan ta kalli Nan din tin kafin tai magana Amah ta lura da Abinda take so taqaraso tana daukan dryer din tana kunnawa ta fara busar mata da kan tana cewa "Sorry" Thank you tace da muryanta me sanyi tana tambayar Aman kwananta nawa a asibiti. Fada mata Amah tayi tana sake mata sannu batareda ta sanar da ita qarin komai ba sbd suma basusan menene yake damunta ba dan kuwa ciwon nata bayan familyn da doctors dinsu babu wanda yasan menene ya sameta. Ana gama busar mata da kan ta miqe ta shirya cikin oversize Cardigan din balenciaga da dogon wandon balenciaga din shima wanda yakeda fadi sosai tai sallah tana idarwa ta sha tea din da aka kawo da cake kadan take taji ta sake gajia dan haka ta nufi gadonta ta kwanta take bacci ya dauketa na gajia. Kaf familyn gidan babu wanda ya fito sai yamma sosai suka fara fitowa kowannensu yayi wanka da sallah sun saiyo kayan jikinsu. Asalin limited edition designers suke duka a gidan wanda ake zuba ba qananun kudi ba ana siya, A rayuwarsu kaf basusan wani abun ba bayan asalin designers na amfani dashi, Takarman takawarsu kadai kudadensu wani budget dinne na rayuwar wasu ta shekaru bare watches nasu dasu sakawa na manyan dollars da basusan zafinsu ba, Sutura kuwa baa magana sbd ajinsu ma kadai ya isa ya nuna menene a jikinsu dan haka gaba daya ZAADENs babu wanda closet dinsa kudinta vazata budewa mutane da dama sabuwar rayuwar da shima zai budewa wasu da daman ba. Jannah zaaden kanta datake qaramarsu babu abinda ba designer ne a kayantaba ko abin amfaninta dan ko lipsticks dasu liner da cosmetics nata designers ne,su skin products nata ma kansu basuma san akwai wainda ba designers dinba dan haka koda ta taso batasan komai ba bayan luxuries kawai. Itace tafara saukowa tana kokarin nufar dakin Mimi saiga Mimin ta sauko daga bangaren dad tareda dad din yana ganinta ya miqa mata hannu ta qaraso ta kama hannunsa tace "Dad You look tired" Murmushin karfin hali yayi yana cewa "And you look pale Jannah Zad" Murmushi tayi itama tana kallan Mimi dake murmushi itama. Qamshim Maheer Zad ne ya sakata juyawa tana kallan hanyar fitowarsa sai gashi ta riga ganin Ammar daya fara fitowa qamshinsa na gaurayewa dana Maheer din yayi wani irin fresh na dan hutu da nutsuwan daya samu na yau din. Kallanta yayi da fararen idanuwansa yana sake mata wani Murmushin daya sakata sakin dad dinta ta dawo gurinsa tana masa murmushi itama tana cewa "My AmZad looking calm" Murmushi me sauti ya sake yana cewa "Yaya kikeji?? Just tired amma lafiya kalau. Dining suka nufa wanda yake cike abinci da snacks da teas kala kala da fresh juices da cutlerys masu tsada da kyau. Zaunawa sukai bayan Dad ya zauna Amah ce kadai takeda damar zuwa idan suna cin abinci dan cikin kaf masu aikin dan haka tana tsaye a gefe koda suka zauna ta matso tafara serving nasu a natse kuma tasan abinda kowannensu yake ci da yawan yanda yakeci. Cikin nutsuwa sukaci abincin suna gamawa suka wuce Sallah. Suna dawowa sallah a palon Dad suka zauna dukansu suna fira kaman yanda suka saba sunata kokarin hana Jannah sanin menene yake damunta har ta fara jin bacci sosai Saleem ne ya rakata har dakinta kafin ya wuce nasa dakin daga can. Washe gari Maheer yafara fita office hakama saleem ya koma school Ammar kuwa a gida ya wuni bai futa koina ba yana tareda jannah da Mimi da dad. Sai da akai kwana biyu dad ma ya warware ya koma Dzad dinsa ya fara fita office Ammar kuwa saida ya share sati biyu kafin yabi flight ya kom makaranta. Jannah ta koma school itama sedai ranar datai sati biyu da komawa a school ta fara samun matsalar shortness of breath daya ringa sakata collapsing. So biyu tana samun hakan sai school suka bata hutu sedai tana samun hutun sai gashi bata sake samun matsalar ba sai aka lallaba taci gaba da zuwa school. Ko wasu kwanakin masu yawa bata sake ba ta samu attack daya saka zuciyarta kasa dauka ta yanke jiki a school din a rikice akai asibiti da ita sedai su Dad suka sameta a asibiti kaman yanda take wancan karon haka ta share kwanaki a kwance da oxygen kafin kafin Allah yasa ta farfado. Hankalinsu bai qara tashi ba suka shiga asalin damuwa da tsoro da firgici saida ta ringa samun collapse a school wanda ta saka akan dole tasan Asalin menene yake damunta tayita kuka sbd ganin mutuwa zatai tabar iyayenta da yan uwanta. Kuka da halinda ta shiga ya saka ciwonta tasowa sosai wanda ya sakata kwanciyar kusan sati biyu bata san wanda yake kanta ba. A wannan lokacin ne Dad yasan dukiyarsa ba komai bace hakama shi din ba kowa bane a gaban ikom ubangijinsa dan haka ya rufe kansa a daki ya ringa rokon Allah ya rabasa da duk abinda ya mallaka ya bar masa Jannah din. Mimi ma tayi kuka ta fadawa Allah daga karshe ta dangana ta barwa Allah ikonsa sbd ganin duk mazan gidan babu wanda yakeda jarumtar halinda Jannah din ke ciki sai ita ta koma tafisu karfin hali da mamakin irin yanda Allah ya jarabcesu da yiwa jannah so mafi girma akan komai banda ita datake jin ma ko acikin yayanta tafi kaunar Ammar dan haka ta koma tafi su karfin hali da jarumta akan ciwon na jannah sbd ta saddakar tasan jannah bame tsawon rai bace. Jannah a cikin qanqanin lokaci Allah ya maidata abar tausayi babu abinda dukiya da gatanta zasuyi mata sai yanda Allah yaso yi da ita. Kallansu dr Abraham yayi a karo na ba adadin zaman sharawa dasu ya fara koro musu bayanin, "Yawan collapse datake samu yana qara tsananta raunin zuciyarta dake failing wanda kaman kwanakinta na raguwa ne sa sauri, Ya kamata a kiyaye sosai tareda nesantata da doguwar hayaniyar da zata ringa ma sakata tinane tinanen dasuka fi karfin kwakwalwanta datake bawa zuciyarta stress" Cikin sanyi Ammar ya kalli dr Abraham din ba kuzari a muryansa yace "Wat happens wen the heart fails??? Da sauri dukkaninsu suka kallesa banda Mimi data ita likitan ta kalla wanda yayi shiri kafin ya sauke ajiyar zuciya da numfashi me sanyi yace "Bama fatan hakan Mr Ammar Zad,.... Kallan dr yayi da idanuwansa da sukai jajir ya sake bude baki yace "Ina tambaya ne sbd we cant lose her, She has to liv,i cant lose someone again sbd zuciyar da ake buqata, Meyasa bazaa saka mata zuciyar duk wanda aka samu ba.... Mimi ce tayi saurin riqesa tana kallansa cikeda mamaki da fargaba tace "Ammar,me kake fada?idan ana samun hakan da zayneb tana tareda mu yanzu Zuciyar mutum ake magana ba qaramin abu ba, Samunta abu ne me wuyarda sedai mu dauki dangana mu barwa Allah zabi mu gode da lokacin da suka rage mata a duniyar muyi Appreciating hakan..... Ta qarasa zancen idanuwanta na cikowa da hawayen da batasan su gani. Dad ne ya dago ya kalleta tana fadar abinda yakejin shima kaman bazai iyaba, Ammar kuwa dr Abraham ya kalla cikin rashin ja da baya yace "Heart transplant shine kadai abinda take buqata ta rayu right Dr?? Gyada kai dr Abraham yayi yana rarraba ido a tsakaninsu ganin dukkaninsu sun sauke jajayen idanuwansu akansa suna jiran amsarsa. Maheer ne ya matso shima cikin karfin zuciya da kasa yadda da zasu iya kallo har zuciyarta tayi failing gaba daya ta rasa ranta yace "Wat are the chances?? "with the right matching donor,90 percent" Da sabon mamaki da wani irin shock din samun qwarin gwiwa me karfin gaske na zancensa suka kallesa Maheer na maimaita 90 percent din cikin farin ciki. Dad ma dagowa yayi ya sake kallan dr Abraham din yana neman qarin bayani. Dr Abraham ya jinjina musu kai yana cewa "Idan aka samu donor datai matching zata rayu insha Allah cikin aminci kaman kowa, Sedai samun donor na zuciya abu ne me wuyar gaske sbd candidates are placed on a national waiting list so kafin ma ta samu time dinta zai iya cikawa Hakama donors na wuyan samune sbd yawanci masu donating sai wainda suke fama da brain injuries ko wainda ke gabanin mutuwa." Katsesa Dad yayi da cewa "Zuciyan da zaa dasa mata kawai ake buqata right? Yes but se wanda zaiyi matching" Maheer ne da Ammar suke hada baki gurin cewa "Zata samu zuciyar da zaa dasa mata kuwa kota yayane koda hakan na nufin zasu rasa komai. Mimi saurin kallansu tayi sedai Dad baima bari tai magana ba yace saleem ya tafi da ita kawai. Dad numfashi me sanyi ya sauke sbd a yanzu kam baisan komaiba bayan neman zuciyar da zataiwa 'yarsa kota waye yana so a shirye yake barar da dukiyarsa gurin nema. Maheer ma a nasa bangaren ajiyar zuciya ya sauke sbd a yanzu bayajin sunada buqatan sake bude wani kamfanin bayan na asibitin da zasu nemarwa kansu zuciyar da suke buqata. Ammar ma jin yayi wani sanyi yana mamayesa dan kuwa koda zai karar da komai nasa ne saiya nemowa Jannah matching din da zatai mata sedai kuma sbd yanda yake da natsi da son sanin komai akan matsalar Mahaifiyarsa data rasu da jannah yana buqatan neman ilimi akan ciwon dan sanin komai da kansa baya buqatan kowa nai masa bayanin komai da kansa yakeson sanin komai. #MAMUH #ZADEENS #LIMBAS ZAFAFA BIYAR KALBIM 500 mamuhgee A DUNIYATA 500 Huguma AJIYA A DUHU 500 Billyn Abdul KIRJIN ME HANKALI 500 Miss xoxo Pay at 0022419171 AccessBank Maryam sani gummi Shedan biya 09033181070 Or mtn vtu at 09032345899*_Arewabooks@Mamuhgee_* 17 *ZUZEAM VENTURES* Best APHRODISIAC 08144015291 Aslm barkanmu da wannan lokaci Ina Mai farin cikin sanar daku cewa Zuzeam ventures takawo maku ingantattun magunguna masu inganci cikin Aminci Muna da kaya kamar haka Mallaka Maganin sanyi Maganin cire tumbiMaganin farin jini Maganin matsiMaganin mata Maganin sa ni’ima da dandano Dulka Amare Set na gyran jiki Set na amarya Tabaje tsumin Gomba Xuma kiba ta hips and Brest Magungunan gyran Brest Magungunan Karin hips Maganin sliming Muna da kaya masu inganci cikin sauki da rahusa Ina wadda keneman mallaka sahihiya quaranty wlh hajiya kixo ga zuzeam ventures xakiji ddin mallaka duk fadin ran ogah duk fadansa wlh sai yyi sanyi 08144015291 Idan maganin mata kikeso akwai Idan gyran jiki kikeso gyran fata gyran Brest magungunan sa kiba da hips DOMIN samunta Kai tsaye kira wannan no 08144015291 DOMIN mgn da ita whatapp 08144015291muna tura kayanmu ko ina cikin iKon allah 🥰👌🏻 Bononza Bononza Tsimin mangoro 1k🥭 Tsimin dabino 1k Gumba ukku balai 700 Gumba aya da nonon rakumi 700 Garin kafi ciccibi 500 Garin bata gaban kishiya 500 Matsin mallaka tada zaune tsaye 2500 Turaren mallaka ba aba mai kishiya 2500 Total kayan 9500 Za a bakisu akan 3800 Kuma mutun goman farko nadakyautar Abun 2k 🗣️🗣️🗣️🗣️🗣️🗣️ ASSALAMU ALAIKUM ALHAMDULILLAH YAN UWA NEW PROMO YA KAMMALA💃🏽💃🏽💃🏽😁😁😁 da 5k dinki ki kwashi kayan 12k hajiyata 💃🏽💃🏽💃🏽😃🙃Kazar gadali ta mallara Rabi 3500 Tsimin gam gam 1500 Ruwan kara zunzurutun dadı😋800 Garin 7in1 1k Gumba 3 balai 500 Gumba kwakwa da dabino 500 Infection ruwan tsarki 1k Garin zunzurutun dadi 1200 Matsin ba a fira d wando 500 Matsin infection mai matse mace gam 500 12k All at 5k kedai dannan link dinnan don samun naki ki maza kiyi bucking koda kudinki saida Rabonki ********** Mimi suna dawowa gida kasa shiru tayi ta kalli dad wanda fuskansa take a hade ba alamar bata fuskan maganar ma da duk take son yi wadda ta danganci cewa a hakura a zuba ido batareda kokarin komaiba Jannah kwanakinta su qare bayan Allah ya basu damar da zasu iya samar mata lafiya ta rayu. Duk da rashin bada fuskansa Mimi daurewa tayi itama ta bude baki tace "Me kuke nufi da nemo donor kota halin yaya? Dzad zuciyar mutum fa ake magana ba wani abinda zaa iya zuwa kasuwa a siyo ba... Maheer ne ya katseta da cewa "Mimi ki dena maganar zuciyar mutum kaman wani abinda bazaa iya samuba, Kina sanesa yanzu ma da kudade ana siyan mutane ko nawa kakeso?? Jiyowa tai tana masa wani kallan mamaki da takaici tace "To wainda suke siyan mutanen suna siyansu ne dan rabasu da wani abin a jikinsu ne??suna siyansu ne dan bauta da wani aikin wahalar daban Kadama ka sake kawon wannan zancen dan ko anayi mu meza muyi da safarar mutanen? Sai alokacin dad ya dago yai mata wani kallo yana mamakin zancen dayake fita a bakinta na rashin tinani da nazari. Bai samu damar tankata ba dan maganarta ma hanya take safarar mutanen zasu fara babu abinda yasha masa kai indai sa kudi ake safarar baida matsalar wannan. Maheer ma kallan dad din yaga ko kallo mimin ma bata ishesa ba dan haka ya dawo da kallansa kanta yana cewa "Mimi pls ki bari zanyi handling komai a yanda ya kamata batareda abinda kike tinanin ba" Wani kallan ta sake masa kafin tayiwa Dzad din ta juya tabar palon tana mamakin tayaya suke tinanin neman abinda Allah ne kadai yake halitatta ba kaman abinda ake siya bane tinda da kudin na siyan zuciyar da zayneb kila tana raye. Ammar dayake zaune palon bai samu shiga zancenba sbd Abinda yake karantawa a laptop yana dafe goshinsa dayake jin kaman kansa zai rabe biyu sbd tinane tinane da abubuwan dayake ji cikin kan. Juyowa Maheer yayi ya kallesa zaiyi magana Dad ya hanasa yace ya kyalesa sbd yasan Ammar din shima bazai iya bari Jannah ta rasa donor ba kota halin yaya. Numfashi me zafin gaske Ammar din ya sauke yana dago idanuwansa da suka sauya ya fara kallan Maheer kafin ya dawo da kallansa kan dad dayake jiran Abinda Ammar din zai fada. "Dad ina son zama cardiologist, Zan fara daga farko,inason sanin komai akan abinda ya shafi zuciyar dan adam... Maheer kallansa yayi da sauri jin zai koma baya a karatunsa dayake kammalawa. Dad kuwa ajiyar zuciya me sanyi ya sauke wani nauyi daya danne kirjinsa yana sauka sbd abinda yake tsananin buqatan kenan a cikin yayansa dan kuwa suna buqatan sanin abubuwa akan zuciyar da suke nema ta hanya me kyau da mara kyau dole saida nasu dan bazasu bari likitoci su zama sune zasu ringa sani da sanar dasu. Maheer kuwa shiru yayi yana nazarin zancen sbd idan har waninsu yayi likitanci sbd hakan matsala zata iya zuwar musu gaba sbd career dinsa zata iya lalacewa har abada da hakuncin da duk kudinsu bazasu iya kubutar dashi ba,babu abinda yafi musu irin su samu kwararrin doctors din da zasuyi aiki dasu wainda daga baya ko careers nasu sun lalace zasu basu kudade masu yawa ne kawai su kama gabansu tinda su buqatansu ta biya. Dan haka kallan dad yayi yana zaunawa cikin nutsuwa yafara cewa "Dad Ammar baya buqatan sauya career dinsa akan wannan matsalar, Hakan is very risky ga rayuwansa da zaadens gaba daya, For this All we need professionals kuma best cardiologist wen we got abinda mukeso shikenan ba ruwansa da abinda zai iya biyowa baya, Aiki ne da zaayi without leaving any traces so the best abu da zamuyi a hakan shine hana family ko daya zama cikin aikin." Dad ma yayi tinanin hakan tin kafin Maheer din ya fada sbd bazai bari sunan zaadens ya fito a duk wani barnan da zaayiba amma kuma yana tsananin son wani a cikin nasu yasan komai akan hakan indai samun zuciya wa jannah zaiyi wuya to tabbas saisun zaba boyayyar dirty hanya. Ammar cikin tsananin son karantar duk abinda ya shafi zuciyar ya bude baki baki yace "Idan har zamu samu abinda mukeso daga baya sai ayi tinanin yanda zamu fita clean but dad i really need to be a cardiologist ba akan Jannah kadaiba har akan wanda zamu samu gaba a family me wannan ciwon, Mun rasa Mum we cant l... Kasa qarasawa yayi sbd bama zai iya tinanin rasa Jannah ba. Maheer ma cikin dagewa da nasa zancen yace "No Ammar bazai yiyu ba,ba lallai sai kayi karatun ne zaa samu yansa akeso ba bama fatan ma har ka kammala karatun baa samu yanda akeso ba" Hayaniya ce take neman tashi a tsakaninsu duk da Maheer din yana gaban Ammar din sosai amma Ammar sam baida niyar fasawa sbd jin yake ko bayan rasuwar Mum dinsa tabbas yanason karantar ciwon da yayi ajalinta sbd yaji irin azabar data shiga a lokacin jinyarta da yanaji yana gani sedai ya kalleta a kwance bata cewa komai ciwone kadai yake cinta bata ko iya Hayaniyar azaba. Hakama a yanzu da jannah take cikin irin wannan yanayin babu wanda yasan abinda take ji sai Allah daya doro mata ciwon dan haka koda zai rasata itama yanason sanin komai akan ciwon sbd kaucewa rasa wani a agaba. Dad shiru yayi yana sauraronsu kansa na sarawa yana shiga nasa tinanin maganar kowannensu sbd idan har suna son fita clean kaman yanda Maheer ke cewa dole sai Ammar ya shiga ciki dan kada doctors din dazasuyi amfani dasu suyi musu wata hanyar dragging nasu dan haka duka biyun zasuyi, Ammar zaiyi karatu amma ba anan qasar ba hakama duniya bazata san asalin professional dinsa ba. Shiru sukai jin abinda dad din ya fada Maheer shiru yayi yana juya zancen Ammar kuwa bai damu da komaiba idan har zai samu abinda yakeso. Ammar baima tsaya jin wani sabon zancen ba ya fice daga palon dauke da laptop dinsa yana fidda wayarsa dan waya. Maheer dad ya kalla wanda ya riga yayi maganarsa dan haka babu damar cewa komai. Shima miqewa yayi zai fice Dad yace "Ka tabbata an samar masa admission da komai a taqaice batareda bude identity dinsa sosaiba" Numfashi ya sauke a hankali kafin yace "Yes Dad" ya juya ya fice yana fidda wayarsa shima dan saka kira. A tsakaninsu su uku aka bar zancen Mimi da saleem basu sani ba sai Daddy mahmoud wanda ya karbi ragamar karatun na Ammar yace Maheer yabar masa komai. Mimi tin daga lokacin bata sake sanin komai akan ciwon jannah ba sedai idan ciwon ya tashi ayita fama ana lallabawa harta dawo daidai. An sakata a waiting list na neman donors a qasashe daban daban duk da sun zuba wasu irin kudi sun saki akan duk inda suka samu a riga basu sbd akwai wainda suke gabansu duk da ba yawa amma samun ne yakeda wuya sbd da yawa suna rasuwa ne batareda sun samu donors ba wanda ciwon kaddara ne ba kowane yake tashi ba samun donors na zuciya abu ne me tsananin wuya da hadari. A bangarenta ita jannah din ahankali ahankali ta tashi daga yarinya me walwala da farin ciki ta koma yarinyar datake rayuwar nutsuwar jiran cikar kwanakinta da rashin walwala hakama ta koma shiru shiru kwata kwata bata iya hayaniya ko sakewa a cikin mutane, Wani irin tsaro me karfin gaske ake bata sbd koina tana iya collapsing shiyasa a duk inda zaa kaita cikin tsaro take babu daga kafa, Nurse aka daukan mata wadda duk inda zata tare suke tafiya, Damuwa da rashin walwalan datake ciki wanda ya sauya rayuwarta kwata kwata ya saka ciwon yake yawan tasar mata yakuma fara nunawa duniya sbd ta qanqance kwata kwata bata girma ko qara jiki sai haske takeyi wanda hakan ya daga hankalim familyn suka sake duqufa a gurin neman donors tako ina amma babu labari. Ahankali ahankali aka ta dena zuwa school sbd bazata iya ba sunaji suna gani aka tattara karatunta aka ajiye bata fita koina hakama kwata kwata sun boye ciwonta da matsalarta ga duniya iya doctors nasu ne kadai suka sani sai nurse dinta saisu family. Rayuwarta ta tashi daga yar gata ta koma abar tausayi sbd karatu malamai aka daukan mata a gida ake zuwa koyar da ita shi shima baa wani jimawa ake bari sbd yawan gajiya datakeyi. A bangaren Ammar kuwa yana india yana karatu sosai bayaji baya gani ya tattara komai ya ajiye karatun yakeyi sosai ba wasa ya duqufa gashi da qwaqwalwa me gashi kuma ya qwallafa rai dai ya zamana yana samun haske a karatun nasa, Saleem Zad ma yana makaranta yana karatu dan haka sai ya zamana gidan daga Mimi saisu dad ne suka rage suna kulawa da jannah din wadda kallanta kadai yake karya zuciyoyinsu. Maheer sosai ya dage yana kulawa sa companies dinsu yana bin every step na dad da daddy mahmoud wanda yake yawan zuwa duba jannah. A Nigeria kuwa aikin babbar Asibitin da ake ginawa yayi nisa wadda sike tinanin dawowa Nigeria neman donors idan an kasa samu a kasashen da suketa nema. *******lokaci yaja babu wani haske ko sauyi daga ciwon Jannah wadda zuwa lokacin ita kanta ta cire rai daga rayuwar kwata kwata gashi shekaru sun dan ja tana gani abokan karatunta suna nisa a karatu suna tafiya karatu tana zaune gida a killace bata taba samun fita ba sbd duk abinda takeso ko take buqata a gida ake gabatar mata dashi, Ta debo shekarun a cikin rashin walwala da farin ciki bare sakewa, Tsaron da ake bata yayi yawan daya qarasa kashe mata sauran rayuwa da hope datake dashi, Ta rasa shekarun walwalan quruciyarta a tsare cikin ciwo da tsananin tsaron iyayenta, Ta taso batasan me duniyar waje take cikiba, Batasan yaya ake walwala da nishadi ba, Tsaron da ake bata ya koma tamkar horo a rayuwarta data mutu, Tsananin son da ake mata ya koma tamkar gubar datake kashe rayuwarta batareda sun sani ba, Tana ganin irin fadi tashi da matsanancin qunci da rayuwar dacin da ahalinta keyi sbd nemar mata kalbim din da zata rayu dan haka take ganin kanta a matsayin baki da mummunar kaddarar ahalin, Bata kawo musu farin cikin da suke fatar ta zamar musi ba ta zama mummunar kaddadar datake quntata kowanne mutum dayake cikin familyn. Ta cire rai daga rayuwa duniyar takeson ta bari Allah ya dauki rayuwarta ta huta da qunci da ciwon datake ciki suma su huta da gwagwarmayar da babu tabbas. #MAMUH #ZAADENS #LIMBAS #JANNAH ZADEEN #UMMITAH LIMBA ZAFAFA BIYAR KALBIM 500 mamuhgee A DUNIYATA 500 Huguma AJIYA A DUHU 500 Billyn Abdul KIRJIN ME HANKALI 500 Miss xoxo Pay at 0022419171 AccessBank Maryam sani gummi Shedan biya 09033181070 Or mtn vtu at 09032345899*_Arewabooks@Mamuhgee_* 18 *ZUZEAM VENTURES* Best APHRODISIAC 08144015291 Aslm barkanmu da wannan lokaci Ina Mai farin cikin sanar daku cewa Zuzeam ventures takawo maku ingantattun magunguna masu inganci cikin Aminci Muna da kaya kamar haka Mallaka Maganin sanyi Maganin cire tumbiMaganin farin jini Maganin matsiMaganin mata Maganin sa ni’ima da dandano Dulka Amare Set na gyran jiki Set na amarya Tabaje tsumin Gomba Xuma kiba ta hips and Brest Magungunan gyran Brest Magungunan Karin hips Maganin sliming Muna da kaya masu inganci  cikin sauki da rahusa Ina wadda keneman mallaka sahihiya quaranty wlh hajiya kixo ga zuzeam ventures xakiji ddin mallaka duk fadin ran ogah duk fadansa wlh sai yyi sanyi 08144015291 Idan maganin mata kikeso akwai Idan gyran jiki kikeso gyran fata gyran Brest magungunan sa kiba da hips DOMIN samunta Kai tsaye kira wannan no 08144015291 DOMIN mgn da ita whatapp 08144015291muna tura kayanmu ko ina cikin iKon allah 🥰👌🏻 Bononza Bononza Tsimin mangoro 1k🥭 Tsimin dabino 1k Gumba ukku balai 700 Gumba aya da nonon rakumi 700 Garin kafi ciccibi 500 Garin bata gaban kishiya 500 Matsin mallaka tada zaune tsaye 2500 Turaren mallaka ba aba mai kishiya 2500 Total kayan 9500 Za a bakisu akan 3800 Kuma mutun goman farko nadakyautar Abun 2k 🗣️🗣️🗣️🗣️🗣️🗣️ ASSALAMU ALAIKUM ALHAMDULILLAH YAN UWA  NEW PROMO YA KAMMALA💃🏽💃🏽💃🏽😁😁😁 da 5k dinki ki kwashi kayan 12k hajiyata 💃🏽💃🏽💃🏽😃🙃Kazar gadali ta mallara Rabi 3500 Tsimin gam gam 1500 Ruwan kara zunzurutun dadı😋800 Garin 7in1 1k Gumba 3 balai 500 Gumba kwakwa da dabino 500 Infection ruwan tsarki 1k Garin zunzurutun dadi 1200 Matsin ba a fira d wando 500 Matsin infection mai matse mace gam 500 12k All at 5k kedai dannan link dinnan don samun naki ki maza kiyi bucking koda kudinki saida Rabonki ************** A lokacin da ta cika shekaru goma sha shida Ammar ya gamo karatunsa ya dawo a matsayin cardiologist doctor sedai hakan bai sauya komai dan kuwa har lokacin baa samu donor ba. Duk yanda sukeso su saka farin ciki da walwalwa a rayuwarta sunyi amma babu haske ko kadan sbd ta riga ta saka kanta a duhu da dacin da babu fitowa hakan kuma yana tsananin qona zuciyoyinsu dan haka Mimi ta ringa ganin ta nuna musu su hakura abarwa Allah a jira lokaci kawai wanda kuma yana kusa tinda ciwon nata yayi nisan da yanzu ba iya qunci kadaine yake dabaibaiye da ita ba hadda ciwo sbd tayi weak sosai batada kuzari kaman kowa. Dr Abraham ne kwatsam yakira dad kai tsaye ya sanar dashi sunada wata patient datai nisa kuma yana saka ran zuciyarta kila zatai matching. Dad na jin hakan daman ba qananun kudi yake sakarwa Dr Abraham ba akan a samar masa zuciyar koda ta patients dinsu ne idan aka ga sunyi nisa. Akwai patient biyu da dr Abraham din yayi sanadin mutuwarsu sbd zuciyarsu sedai rashin saar da akeyi familynsu basa yarda suyi donating zuciyarsu wadda daga karshe suke mutuwa a banza batareda an samu cirewa. Wannan karan ma Dad numfashi ya sauke yana cewa "Idan ka tabbatarda wannan din zaiyi matching kayi treating patient din ko nawa ake buqata zaa biya ya warke ka sallamesa zamu bibiyesu mu samu heart din daga baya sbd suma ana magana ko yayi nisa ba zasu yadda ba, Idan har zaiyi ka tabbata a nemar masa lafiya kawai" Ajiyar zuciya dr Abraham yayi yana yadda da shawaran Dad din sbd tini suka gama da rayuwarsa ta hanyar sakashi a jikinsu kudi ne kawai yake duka kaman zaaden dinne shima dan haka babu abinda baya musu. Ammar na jin an samu wadda xatai matching ya kasa nutsuwa da kansa ya ringa taimkawa da familyn yaron da kudi sosai yana shiga jikinsu su kuwa suka aminta dashi sbd yanada kwarjini da kwantar da kai. Dr Abraham ma kulawa da sakewa ya ringa yi dasu a matsayin caring doctor. Yaron baida uba mum dinsa ce kawai sai sisters dinsa biyu yan asalin Ethiopia ne. Familyn Nuhan da zaadens kusanci ne da kauna me karfi ta shiga tsakaninsu da dr Abraham wanda ya nunawa familyn Nuhan Zadeens nada tsananin tausayi ne kawai da son yara sbd basada yara sosai shiyasa suke taimaka musu sosai duk da suma sunada nasu kudin amma sbd son kusantar su ZAADENs din da kuma burin ganin yayanta mata sun samu shiga familyn sbd ganin Ammar da maheer sai mahaifiyar nuhan din ta sake dasu sosai tana sake shige musu sosai. Maheer kuwa da yarta daya yayi amfani ya san komai na familyn da irin karfin dasuke dashi wanda ko zai iya kawo musu matsala ya gama sanin komai nasu ya fahimci basu da wani power ko hanyar samun powern dan haka ya janye mata. Duk kusancin da suka samu familynsu nuhan basu san zadeens nada wata 'yar ba sbd kwata kwata sun boyewa duniya ita tini. Nuhan yaji sauki sosai sbd taimakon su Dad din da suka zubarda kudi sosai aka n3ma masa lafiya. An sallami nuhan din ko wata biyu bai rufa ba Daddy mahmoud ya iso qasar Kwana hudu da zuwansa Aka kira familyn nuhan aka sanar dasu ya samu Mummunan accident da sabuwar motar da Maheer yayi masa kyauta anata murna. Irin yanda yayi accident kwata kwata kwata yayi damage dan haka su Maheer ne sukai family tinda sun zama daya akai asibitinsu dr Abraham dashi. Suna isa akai ciki dashi cikin gaggawa tareda Ammar wanda yake cikin likitocin da zasu basa taimakon gaggawa. Babu tausayi babu komai dr Abraham ya shiga tiyata da dashi tareda Ammar da babban 'dan Dr Abraham din wanda yake qwararran likitan zuciya. Zuciyar Nuhan suka cire wadda take bugawa ahankali suka dinkesa tareda gurare da dama a jikinsa sbd munanan raunikansa da harma inda baiji raunina sun yanka sun dinka sbd hana na kirjinsa ya zama daban. An fito da Nuhan wanda baiyi surviving ba ya rasu tin a gurin aiki suka rubuta Take mahaifiyarsa ta yanke jiki ta fadi a gurin hakama sisters dinsa dole su Maheer ne sikai komai tareda saka hannu a takardun karban gawar da sauran formalities din. A cikin qanqanin lokaci akayo asibitin da Jannah da daman komai anyi mata a shirye take da karban donor din. Abinda basu saniba shine suna nasu allah yana nasa koda aka shirya komai zuciyar Nuhan ta dena bugawa ta mace itama dan haka daga Ammar din harsu dr Abraham kaman zasu zare sukaji. Dad ma jin yayi kaman zuciyarsa zata fashe sbd duk wahalar da sukai ta tashi a banza. Maheer ma kasa hakuri yayi ana gama komai na janazan nuhan ya tahowansa goda ya rufe kansa a daki. Ammar ma kasar ya bari tareda daddy mahmoud. Gabaki daya zadeens shiga zaman makoki sukai kowa zuciyarsa qunci da daci wanda Mimi da familyn nuhan suka dauka dik rashin nuhan dinne. Rasuwar Nuhan da wata daya aka suka sake samarda wata matching donor din a porthacort wanda daddy mahmoud ne ya samo shima namiji ne ba tausayi suka tattaro duka familyn suka taho cewan hutu da business tripaka sanarwa Mimi da jannah din. Dr Abraham da Dr finn daban suka taho qasar sbd aikin kawai. Ba tausayi akai damaging brain din saurayin da iyakacinsa shekaru sha tara zuwa ashirin aka zare tasa sedai kuma shima kafin ayi aikin aka rasata wanda daga yanayin brain damage daya samu ne kafin acireta. Wannan karan kusan dukkaninsu kusan bugawa sika kusan yi sbd tashin hankali da masifar dasuke jin kansu a cikinta. Haka shima yaron akai accident dashi can aka tsinci gawarsa aka nema iyayensa aka miqa musu. Ko sati biyu basuyiba suka tattara suka bar qasar. Haka suka dawo suna ci gaba da nema, Tin suna dauken daddaya har yakai da karfin gaske suka ringa neman donors, Ahankali ahankali suka ringa aikin barnar da tini tausayi da shakka ta cire musu basa tausayin kowa akan abinda suke so, Tin suna aikata hakan akan son zuciyarsu harya zamana sun hade kai da DIKKO DILLA wanda yake asalin safarar mutane yana kaiwa qazaman qasashe suna siyarwa a bayi kokuma aikin bautar ginar baqin mai da gurbatacciyar business. Kudi sosai suke bayarwa idan anyi safarar mutane ankai qasar da zaa kai acan zaa ringa auna mutanen da akai safara har asamu wainda ake saka ran zasuyi a hakan mutane da dama suka rasa rayukansu maza da mata masu qananun shekaru batareda su kuma sun samu abinda suke so ba. Ranakun qunci da damuwarsu da tsoron rasa abinda suke tsananin so sai qaruwa sukeyi sbd Jannah sai nisa takeyi a yanzu ta koma da oxygen ma take rayuwa koyaushe a hancinta dashi take komai sbd nisan datake qara yi. ******ZADEENs HEALTH CEN ta kafu a Nigeria inda sukeda manyan branch biyu lagos da Abuja, Asibitine na kudi sosai data tsaru ta hadu tamkar baa Nigeria dinba, Basa qasar amma asibitin nasu ta karbu tayi suna sbd taimakon da ake badawa sosai a asibitocin kyauta ga marasa karfi wanda hakan ya saka tai fice tayi suna ga masu karfi da marasa karfi. A wannan lokacin ne kuma Maheer yayi aure da wata qwararriyar Nurse Yar Nigeria dake zaune a Sidney din. Ya aureta ne sbd ta hanyarta suka samu donors kusan guda uku amma basuyiba tanada kyau da ilimi sosai tareda tsananin son kanta itama ga duk abinda takeso hakama kai tsaye yaji yana sonta kaman yanda itama taji yayi mata sbd indai zata samu duniya da jin dadin dayake cikinta kamar zamowa sirikar zaadens to babu abinda zai dameta da abinda sukeyi hakama iyayenta su kawai abinda suka sani shine idan suka zama family da zadeens shikenan basa buqatan komai kuma. Anyi auren Maheer da Aneesa wadda suke kira Anny ta ajiye aikinta kawai dai sedai a cikin gida basa buqatan kowace nurse me kulawa da Jannah yanzu itace take dubata dan haka sai jannah da ciwonta suka sake zama sirri ga mutanen duniya. Sun zabi boye jannah da ciwonta ne ga duniya sbd barnarsu bazata taba fitowaba hardai yanzu da sun riga sunyi nisan da basa jin kira, Babu wani tausayi daya rage musu na duk wanda basuda jini dashi dan haka a tsaftace suke barnarsu batareda da sanin duniya ba hakama Mimi ma kwata kwata batasan mummunan abun da ahalinta suka zama ba, Saleem dayake yaro a cikinsu kwata kwata shima baya cikin abinda akeyi din amma kusan shima a garesa ko yayane idan zaa samowa Jannah zuciyar da zata buga a kirjinta ta rayu kaman kowa to bai damu da yanda zaa samotaba duk da bai taba kawo a kansa cewan Kisan gilla ake aikatawaba dan nemowa jannah tata zuciyar. Shigowar Anny familyn sai ta zamo a cikin wainda ake barnar da ita duk da bata taba saka hannunta ba amma komai ta sani kuma itace ke hana Mimi gane komai koda taso ganewan sam Anny bata barin ma tasan me duniyar take ciki, Hakama itama tana amfani da nata recourses din gurin nemo donors, Iyayen Anny Dadynta shima yanada rufin asiri sosai sedai baida power da karfin ikon dukiyar da zadeens suke dashi kuma shima yanada gurbatacciyar business dinsa ta boye dayake yi ta baqin mai da harkan Mining dasuke a boye dan haka ba bata lokaci ya sake hadewa da Zadeens dik da dukiyarsu baa gurbace take ba da komai sedai jinin rayukan mutane dasuke hallakawa sbd tsananin son zuciyar data rufe da tsatsar son kai mara amfani. Tsananin kauna da son dayake tsakanin Ammar da jannah ya saka Mimi rokan  daura musu aure da dan lokacin daya ragewa jannah din. Dad sbd takaici da baqin cikin maganganun mimi da koyaushe basuda dadi jin yakeyi inda zuciyar Mimin zataiwa jannah babu abinda zai hanasa rabata da ita ya sakawa Jannah. Ammar da kansa ya zabi bazai taba auren jannah a hakanba saita samu lafiyarta ta samu ilimin da ciwo ya hanata samu ta zamo abinda sukeson ta zama tukuna zai aureta da bugun gaba. Dad kuwa da maheer kwata kwata basa shaawar auren nasu sbd Tsananin kaunar da sukewa kowannensu basason auren yazo ya sakasu jin Ammar ba nasu bane dan a jininsu suke jinsa. *****Kaddararsu gabaki daya ta sauya ne daga lokacinda Ammar ya fara tattarowa ya dawo Nigeria tareda dr Abraham da dr finn a matsayin manyan likitocin asibitinsu. Dr Abraham da dr finn basu ji komaiba daga baro qasarsu suka dawo Nigeria sbd a cikin hutu da daula sike ko a Nigeria din sbd suma sun riga sun zama zadeens dan kuwa babu abinda yake boye a tsakaninsu. #MAMUH ##BESTSTORY #BESTLOVE #BESTSTORY ZAFAFA BIYAR KALBIM 500 mamuhgee A DUNIYATA 500 Huguma AJIYA A DUHU 500 Billyn Abdul KIRJIN ME HANKALI 500 Miss xoxo Pay at 0022419171 AccessBank Maryam sani gummi Shedan biya 09033181070 Or mtn vtu at 09032345899*_Arewabooks@Mamuhgee_* 19 *ZUZEAM VENTURES* Best APHRODISIAC 08144015291 Aslm barkanmu da wannan lokaci Ina Mai farin cikin sanar daku cewa Zuzeam ventures takawo maku ingantattun magunguna masu inganci cikin Aminci Muna da kaya kamar haka Mallaka Maganin sanyi Maganin cire tumbiMaganin farin jini Maganin matsiMaganin mata Maganin sa ni’ima da dandano Dulka Amare Set na gyran jiki Set na amarya Tabaje tsumin Gomba Xuma kiba ta hips and Brest Magungunan gyran Brest Magungunan Karin hips Maganin sliming Muna da kaya masu inganci cikin sauki da rahusa Ina wadda keneman mallaka sahihiya quaranty wlh hajiya kixo ga zuzeam ventures xakiji ddin mallaka duk fadin ran ogah duk fadansa wlh sai yyi sanyi 08144015291 Idan maganin mata kikeso akwai Idan gyran jiki kikeso gyran fata gyran Brest magungunan sa kiba da hips DOMIN samunta Kai tsaye kira wannan no 08144015291 DOMIN mgn da ita whatapp 08144015291muna tura kayanmu ko ina cikin iKon allah 🥰👌🏻 Bononza Bononza Tsimin mangoro 1k🥭 Tsimin dabino 1k Gumba ukku balai 700 Gumba aya da nonon rakumi 700 Garin kafi ciccibi 500 Garin bata gaban kishiya 500 Matsin mallaka tada zaune tsaye 2500 Turaren mallaka ba aba mai kishiya 2500 Total kayan 9500 Za a bakisu akan 3800 Kuma mutun goman farko nadakyautar Abun 2k 🗣️🗣️🗣️🗣️🗣️🗣️ ASSALAMU ALAIKUM ALHAMDULILLAH YAN UWA NEW PROMO YA KAMMALA💃🏽💃🏽💃🏽😁😁😁 da 5k dinki ki kwashi kayan 12k hajiyata 💃🏽💃🏽💃🏽😃🙃Kazar gadali ta mallara Rabi 3500 Tsimin gam gam 1500 Ruwan kara zunzurutun dadı😋800 Garin 7in1 1k Gumba 3 balai 500 Gumba kwakwa da dabino 500 Infection ruwan tsarki 1k Garin zunzurutun dadi 1200 Matsin ba a fira d wando 500 Matsin infection mai matse mace gam 500 12k All at 5k kedai dannan link dinnan don samun naki ki maza kiyi bucking koda kudinki saida Rabonki ************** Dawowansu Nigeria da dan lokaci Dr Abraham ya bada shawaran dawowansu gabaki daya anan sbd a yanda yaga rayuwar nan din take samun abinda suke so anan bazai wuya ba duba da kusan koyaushe koina kuka akeyi da yanda mutane suke bata ko ake kashewa dan haka anan komai zai tafi musu a sauki sabanin can da akwai wani irin tsananin tsaro da binciken da zai iya kawo karshensu gaba daya. Wannan ne ya saka gabaki daya Ahalin ZADEEN's sukai bankwana da komai suka dawo Nigeria inda suka bude sabuwar rayuwa. Irin suna da tarin dukiya da manyan matsayin dasuke dashi a can qasashen ya saka cikin qananin lokaci suka samu wata irin power a Nigeria sukai suna musamman daman sun jima da yin sunan sbd tsananin taimakon da suke badawa a asibitocin kauyuka da birni da asibitocin gwamnati ma sai ya zamana anata yabonsu ana kaunarsu. Sam basada sakewa da mutane kaman yanda basa muaamala da kowa sai masu karfin iko, Ammar gaba daya ya koma ya zama volunteer baya wani zama koyaushe yana gurin yawon asibitoci da kauyuka bada taimakon dan nuna tausayi ga mutane wanda hakan ke qara musu wata irin qima a gurin jamaa. Daurewa Ammar yakeyi kawai sbd biyan buqatansu amma kaf dinsu babu abinda suka tsana kaman rayuwa da mutane marasa karfi da sukewa kallan kaman dabbobi. Dawowansu Nigeria yayiwa Mimi dadi sbd Sun samu damar sauyawa Jannah guri da rayuwa, Jannah ganin yanda familyn suka kasa hakura su dangana sai ta fara kokarin bawa kanta qwarin gwiwan rayuwa dan sakasu farin cikin da kusan suka rasa na shekaru. Hakan datai ba qaramin tasiri yayiba akansu dan kuwa farin ciki mai tsanani suka shiga sedai kuma qarasa cire tausayi sukai aransu suka cigaba da farautan rayukan mutane. Ammar ya dena yawon dayake yi sedai ayanzu suna likitocin da suka saka a asibitin gwamnati da manyan na kudi tareda sake kudin da hankali ma baya dauka dan samun zuciya ga wadda haryanxu duk masu musu aikin basu san waye ake nemawa ba dan ko sunanta baa taba fadaba bare wani yaji. ******* Ummitah dake zaune tana dan dafe gefen cikinta dayake mata wani irin nauyin datake jin kamar zai shigar mata wani gurin rintse idanuwanta tayi ahankali tana dan sauke numfashi ahankali. Mama dake gefenta sannu tai mata tana cewa "Kodai zamu tafi asibitin ne Ummitah" Girgiza kai tayi ahankali tana cewa "Aa kila zuwa anjima ko idan nasha magani ciwon zai lafa mun" Kallanta maman tayi tana jin kaman karta bari zuwa anjima su tafi asibitin kawai amma kuma tinawa da ABDULAZIZ yace zai aiko a tafi dasu sbd bayanan yasa ta barta din idan sun tafi kaman yanda ha fada taci gaba da ganin likita acan. Sayyid ne ya shigo gidan dauke da Farar leda a hannu ta Fruits daya siyo mata yana kallanta yace "Yaya dai? Jikin ne? Mama kodai zamu tafi asibitin ne? Cigaba da aikin abinci da maman keyi tayi tana cewa "Eh nace mu tafin amma tace basai antafi ba A bari zuwa anjiman idan bata dena jin yanayin ba sai mu tafin kawai" Wayar Sayyid dince tafara ringing da sauri ya daga ganin Hamman ne yake kira. Yana dauka kai cikeda girmamawa ya gaidasa yana cewa Ummitan ce batajin dadi. Shiru ABDULAZIZ yayi batareda yace komaiba sbd yanda yaji a zuciyarsa a duk lokacinda akace Ummitah batajin dadi wani irin nauyi da daci yakeji ya cike zuciyarsa sbd ganin kaman ya gaza ne har akai mata auren wuri daya sakata a halinda take ciki wanda bata isaba yake gani kwata kwata hakama an sauya masa tsari da burinsa gaba daya akanta dan kuwa duk gwagwarmayarsa da nemansa akanta ne sbd ita ne, Komai dayake son ya zama a rayuwarsa sbd Ummitah ne, Sbd ya inganta rayuwarta ya hanata shiga quncin daya taso a cikinsa, Sbd ya bata farin ciki da gatan da kowanne da zai samu amma a lokaci daya an sauya masa komai an lalata masa rayuwarta ta hanyarda baida zabi bayan karban hakan hannu bibbiyu dan hakan nema ya karbi Sayyid tareda alqawarin inganta rayuwarsa shima kamar qanin dasuka fito ciki daya. Numfashi me sanyi ya sauke tareda bude baki a natse yace "Ku shirya gaba dayanku yau komai dare zaa taho a tafi daku, Karku bari Ummitah tayi komai hakama basai kun tafi asibitin ba, Zanyi magana da Ummitah" Da sauri Sayyid din ya bawa Ummitah waya ta amsa ahankali tareda dorawa a kunnanta ta ambaci sunansa ahankali cikeda kewarsa datake tsananin ji da buqatansa a kusa da ita. Jin sautin muryanta cikin sanyi daya sauka a kunnensa ya sanyasa miqewa ahankali daga inda yake zaune ya nufi bakin window din dakin ya tsaya yana sauke numfashi mara sauti zuciyarsa na sake daukan wani irin nauyi da dacin rashin kasancewansa a kusa da ita a daidai yanzu datake tsananin buqatansa. "Ummitah" ya ambaci sunata ahankali cikeda nutsuwa da sautinda ita kadai yakewa magana ahakan sbd matsayinta rayuwarsa gaba daya daban yake da komai. Hawayene masu dumi suka gangaro mata ta rintse idanuwanta kuka mara sauti na zuwar mata a karo na farko tace masa "Hammah inason ka dawo dan Allah, Hammah inason na haihu a hannunka kaman yanda aka haifeni a hannunka, Hammah ka....... Kasa qarasawa tayi sbd hawayen da suka tsananta mata gudu haka kawai buqatansa take a kusa da ita sbd ita kadai tasan yanda take jin cikin jikinta. Mama da sayyid shiru sukai jikinsu na sanyi batareda kowannensu ya iya cewa komaiba saima tsinkewa da mama tayi tana ajiye aikin datakeyi batareda ta juya ta kallesu ba. Acan bangaren shiru yayi tareda kasa cewa komai dan duk abinda zai samu a aikin daya kawosa ko shine zai qarasa sauya rayuwarsa to tabbas saiya bar qasar ya koma gida a goben nan. Kasa cewa komai yayi ya kashe wayar bayan yace mata ok kawai dan babu me basa umarni yace ok ko yes kawai sai buqatan Ummitah kadai kaf rayuwarsa kuwa a yanzu. Yana kashe wayar kai tsaye ticket ya kira aka siya masa ya shirya komawa gida. Yana gamawa wayar Alh saad ya kira ya sanar dashi a samar masa driver yaje ayau din koman dare ya dauko su Ummitah shima gobe insha Allah zai dawo. Ummitah kuwa tana miqawa Sayyid wayarsa kasa dagowa tayi ta kalli kowannensu sbd sosai takejin jikinta ba dadi. Sayyid da maman ma jin sukai hankalinma yafi karkata ga tafiyar sbd jikin Ummitan dan haka ba wani bata lokaci suka fara bankwana da mutane shima sayyid din gida ya koma gurin iyayensa tareda Ummitah duk da batajin dadi amma hakan ya lallaba suka tafi sukai bankwana sosai kowa na tausayawa Ummitan sbd duk ta sauya ta fara kumbura sosai irin na masu cikin daya fara tsufa. Duka kayansu Mama kyauta tayi dasu tin daga kayan sakawa har kayan amfani da komai, Sayyid ma kusan komai nasa kyautarwa yayi sutaransa kawai ya bari suma basu fi kala biyu ba ya bari. Ummitah kwata kwata bata cikin walwala sbd yanayinta dan haka sayyid da mama suka matsu driver ya iso su tafi sbd akai Ummitan asibiti. Karfe uku na yamma driver ya iso da lafiyayyar motar ABDULAZIZ din aka daukesu daga garin gaba daya bayan sun rabu da yan uwa da abokan arziki ana kukan rabuwa na tafiyar da baa san ranar haduwa ba. Sayyid Mahaifinsa har cikin ransa yakejin sanyin jikin rabuwa dansa namiji daya tal sedai kaman yanda ABDULAZIZ yayi masa alkawarin Sayyid zai zama abin alfaharinsa kuma har abada ya riga ya zama yaya kuma dan uwan Sayyid din ya saka yakejin damuwarsa bin iska. Mama ma tayi kukan rabuwa da yan uwanta duk da batada uwa da uba a garin amma tanajin radadin rabuwa dasu. Ummitah kuwa nauyi kirjinta yayi mata bata iya ko kukan ba sai jajir da idanuwanta sukai mata tanajin ita kam kamar har abada bazata taba dawowa ba ta tafi kenan, Wani nauyin ta sake jin ya danne kirjinta ta dafe kirjinta ahankali tana zubawa mutanen dake musu bankwana a tsaye ido tana rasa tinanin yi. Rufe musu kofar mota akai ta zubawa kofar gidansu idanuwanta da suke sake yin ja... Ahankali aka tada motar aka tafiya ahankali sai alokacin taji wasu irin hawayen da batasan dasuva suna gangarowa akan fuskanta ta rintse idanuwanta ahankali tana dora hannunta akan cikinta dake motsawa da karfi. Shiru sukai babu motsin komai a motar sai sanyin ac dayake ratsasu babu wansa zuciyarsa batai nauyiba sbd Allah ne kadai yasan rayuwar datake gaba tana jiransu. Tafiya sukeyi sosai da gudu akan titi da lafiyayyar motar da basa jin iskar komai bare kuka karfe ko jijjigar karfe sbd lafiyar motar da tsadarta. Qarfe 11 dare suka isa Abuja kai tsaye gidan ABDULAZIZ din aka nufa dasu wanda yake a tsare kaman bana ABDULAZIZ dinsu da suka saniba, Dayake dukkaninsu suna cikin sanyin jiki da damuwar rabuwa da gida basu tsaya kalle kalle sosai ba Matar Alhaji Saad Anty Maryam taxo ta kawo musu mai aikin da aka tanadar musu tareda abincin da zasu ci lafiyayye sai dakunan dasuke na kowannensu da aka nuna musu. Dakin Ummitah shine a can daban palonsa kusa da nasa Master bedroom din Sai dakin Mama dayake dayan palon shima babba lafiyayye dana mai aiki a kusa da nata sai Dakin Sayyid lafiyayye babba da shima yake palon tareda lafiyayyen toilet aciki. A cikin gidan babu wanda dakinsa baa zuba masa komai na jin dadi da tsarin masu kudi ba. Sallolin dayake kansu suka fara yi kafin sukaci abinci ba bata lokaci bacci ya dauke kowannensu har Ummitah dake fama da jikinta gajiya ta sakata baccin dole ciwon na tafiyarsa. Washe gari me aikin gidan ce Fiddausi ta tayardasu sallah dukkaninsu sbd gajiya da sanyin ac ya sakasu wani irin nannauyan bacci. Suna gama sallah babu wanda ya fito duk da Ummitah tana dakin mama a tare suka kwana sbd sabo. Karfe 9 na safe Fiddausi ta gama komai na breakfast da gyaran gidan taje ta sanar musu suka fito cin abinci. Fiddausi ta kaisu har dining ta nuna musu su zauna suka zauna suna kallan gurin dayake kaman wani shagon saida gilasai da qwan lantarki sbd haske da katon madubin console dayake kallansu a gurin. Ba wani abincin da bazasu iya ci bane doya ce da egg sauce sai Pepper meat da kunun gyada dayaji madara. Ummitah ce kuzarinsu da yanayinsu dan haka ganin ta samu warwarewa tana cin abincin ya sakasu sakewa suma sukaci abincin cikin jin dadi da mamakin arzikin da ABDULAZIZ din yake rayuwa a cikinsa duk da bai ragesu da komaiba shiyasa basa cikin yunwa sa kwadayi ko kadan daman can. Suna gamawa Anty maryam na isowa gidan daukesa kayan sakawarsu da aka tanada tin kafin zuwansu. Sayyid ne kadai babu kayansa se ta saka haydar danta ya daukesa ya fita dashi dan siyyyar nasa kayan. Ummitah ta kalla cikeda kulawa da tattalinta sbd sanin wacece Ummitah a rayuwar ABDULAZIZ yasa duk wanda yake kaunarsa to tabbas saiya kaunaci Ummitah ma sosai. Sannu tai mata tareda wuni a gidan tana nuna musu komai tareda debe musu kewa tinda bayanan ABDULAZIZ din. Ko aranar ABDULAZIZ bai samu isowaba dan haka dole anty maryam ta taho gidan da yaranta duka suka sake yiwa su Ummitan wuni suna debe musu kewa tareda kokarin ganin sun sake batareda nuna qyamar ganinsu yan kauye ba. Cikin jikin Ummitah ya saka Anty maryam ringa nuna mata wata irin kauna sosai da kulawa dan hakan ne ma mama taji tana samun nutsuwa da sakewa dasu. #MAMUH ZAFAFA BIYAR KALBIM 500 mamuhgee A DUNIYATA 500 Huguma AJIYA A DUHU 500 Billyn Abdul KIRJIN ME HANKALI 500 Miss xoxo Pay at 0022419171 AccessBank Maryam sani gummi Shedan biya 09033181070 Or mtn vtu at 09032345899*_Arewabooks@Mamuhgee_* 20/21 *ZUZEAM VENTURES* Best APHRODISIAC 08144015291 Aslm barkanmu da wannan lokaci Ina Mai farin cikin sanar daku cewa Zuzeam ventures takawo maku ingantattun magunguna masu inganci cikin Aminci Muna da kaya kamar haka Mallaka Maganin sanyi Maganin cire tumbiMaganin farin jini Maganin matsiMaganin mata Maganin sa ni’ima da dandano Dulka Amare Set na gyran jiki Set na amarya Tabaje tsumin Gomba Xuma kiba ta hips and Brest Magungunan gyran Brest Magungunan Karin hips Maganin sliming Muna da kaya masu inganci cikin sauki da rahusa Ina wadda keneman mallaka sahihiya quaranty wlh hajiya kixo ga zuzeam ventures xakiji ddin mallaka duk fadin ran ogah duk fadansa wlh sai yyi sanyi 08144015291 Idan maganin mata kikeso akwai Idan gyran jiki kikeso gyran fata gyran Brest magungunan sa kiba da hips DOMIN samunta Kai tsaye kira wannan no 08144015291 DOMIN mgn da ita whatapp 08144015291muna tura kayanmu ko ina cikin iKon allah 🥰👌🏻 Bononza Bononza Tsimin mangoro 1k🥭 Tsimin dabino 1k Gumba ukku balai 700 Gumba aya da nonon rakumi 700 Garin kafi ciccibi 500 Garin bata gaban kishiya 500 Matsin mallaka tada zaune tsaye 2500 Turaren mallaka ba aba mai kishiya 2500 Total kayan 9500 Za a bakisu akan 3800 Kuma mutun goman farko nadakyautar Abun 2k 🗣️🗣️🗣️🗣️🗣️🗣️ ASSALAMU ALAIKUM ALHAMDULILLAH YAN UWA NEW PROMO YA KAMMALA💃🏽💃🏽💃🏽😁😁😁 da 5k dinki ki kwashi kayan 12k hajiyata 💃🏽💃🏽💃🏽😃🙃Kazar gadali ta mallara Rabi 3500 Tsimin gam gam 1500 Ruwan kara zunzurutun dadı😋800 Garin 7in1 1k Gumba 3 balai 500 Gumba kwakwa da dabino 500 Infection ruwan tsarki 1k Garin zunzurutun dadi 1200 Matsin ba a fira d wando 500 Matsin infection mai matse mace gam 500 12k All at 5k kedai dannan link dinnan don samun naki ki maza kiyi bucking koda kudinki saida Rabonki ************* A cikin qananin lokaci suka ji suna samun nutsuwa da iyalan Alh saad wanda shima ya shigo sun gaisa har so biyu ya kuma cewa anty maryam da kanta takai Ummitah asibitin taga doctor kafin dawowan ABDULAZIZ. Da safe suke shirin Anty maryam din tazo suje asibiti dan haka a ranar a dakin mijinta ta kwana sbd Shine zai tasheta tinda asuba sufara shiri bare kuma daman Ummitan da kanta ta tafiyarta gurinsa itama mama bata hanaba tinda kila idan ABDULAZIZ din ya dawo bazai barsu guri daya ba sai Ummitah ta haihu ta koma masa yanda yake ganin ya kamata ta koman. Irin tsananin Asalin son da Sayyid kewa Ummitah kusan a duniyarta ABDULAZIZ ne kadai nasa ya fi nasa sbd So me tsaftar dayake mata daga Allah ne shi ya halitta masa shi a zuciyarsa, Kwana yayi a zaune yana kulawa da ita tareda tarairayanta yana jin kaman ya rabata da cikin jikinta taji sauki hakama shi kansa ya shirya bazata sake haihuwa yanzu ba tinda ciwo da wahala cikin yake sata hakama yana tsoron wani abin ya sameta koda agurin haihuwa ne bare ya sani ko Hammanta ABDULAZIZ bazai bari ta sake haihuwa anan kusa ba idanma bai rabasu ba akan sai sun gama karatun dayace zasuyi. Karfe tara suka fito a shirye tsaf suka nufi dakin mama wadda tinda tai asuba bata koma ba tana zaune tana jiran lokacin zuwan nasu asibitin yayi. Dining suka nufa wanda suka ga ancika sa sosai ayau din fiyeda kullum hakama abincin dayake kai a yau an samu sauyinsa. Mama ce ta zauna Sayyid kuwa Ummitah yake kokarin taimakawa ta zauna Ahankali wani irin qamshi me sanyi ya fara shiga hancinsu mai nutsuwa, Ahankali Ummitah ta dakata daga zaunawan da zatai tana dago fararen idanuwanta dasuke sak da nasa ta waiwayo cikin sanyi hancinta da gurin suna sake gauraya da qamshinsa. Sayyid ma qamshin ya sanyasa sakin hannun Ummitan Ahankali yana juyowa sbd Tin ranar farkon haduwarsa da Hamman ya riqe qamshinsa sbd Kaunarsa da Allah ya dasa masa arai shima sbd Ummitah. Inda suke kalla Mama ta juya ta kalla taga mene sbd ita hankalinta da hancinta basu wani bata tinanin qamshinba. Daidai lokacin ya sako kai a natse cikin wani irin kwarjinin daya saka Sayyid sauke kansa cikeda girmamawa yana kasa qure kallansa akansa sbd ba kwarjininsa kadaiba hatta hasken fatarsa datake wani irin shining na hutu da kwanciyar hankali tareda daula datake samu ya saka kyansa yin yawa. Ummitah ce ta qure kallanta akansa tana jin dukkanin jikinta na mutuwa wani sanyi yana sauka zuciyarta yana mamayewa, Batada abinda yafi mata dadin kallo a rayuwarta sama da kallansa a gabanta, Kyansa da asalin kammminsu dasuke iri daya amma shi ya sauya gaba daya komai nasa daban yake da nata sbd rayuwar da inda suke rayuwar ba dayaba, Hasken idanuwansa zuwa dogon hancinsa ta kalla tana rokon Allah ya basa tsari da kariya daga dukkan sharrin kowace mace a duniya. Shima ita yake kallan cikeda wata irin kewanta dake cinsa kaman cikin kansa zai kunce dan haka yana isowa hannunsa duka biyu ya bude ya rungumeta yana karanta mata adduoin tsari da kariya itada abinda yake cikinta kafin ya saketa ya saki wani Kyakkyawan murmushin daya saka sayyid kasa dena kallansa da tattausan sauti yace "Sorry Ummitah ABDULAZIZ, Yaya,ya jikinki? Kafin ta amsa gurin mama ya juyo cikin kulawa da sakewa da girmamawa yace "Barka da safiya Mama, Yaya fama da sauyin guri? Na sameku lfy?? Murmushin farin cikin ganinsa tayi tana cewa "Duk lafiya kalau Sauyin guri kuma ai munata kokarin sabawa, Tafiyar dare kayi kenan? Zaunawa yayi Ahankali yana cewa "A cikin dare na iso sai ban tasheku ba tinda kun riga kuna hutawa" Sayyid ma zaunawa yayi yana cewa "Barka da dawowa" Kallansa yayi cikin kulawa da sakar masa fuska sbd ya sake yace "Thank you,yaya kaima kanata fama da kadaici right? Gyada kai Sayyid yayi yana kokarin sakewa da hamman. Ummitah na gefensa fuskanta cikeda da murmushi me kyau da nutsuwar data kwana biyu bata iyawa sbd yanayinta. Breakfast suka fara cikin kokarin sakewa dasu dukkaninsu sbd sayyid ya sake dashi tinda tsakaninsa da mama da Ummitah babu wani kamewa ko rashin sakewa. Bazai taba tina yaushe Zuciyarsa ta samu asalin farin ciki irin wanda yake cikinsa a yanzuba sbd kasancewarsa dawowa rayuwa a guri daya da Ummitah wadda babu ranarda zasu sake rabuwar gurin rayuwa daban daban har abada sedai rabuwar kwanaki na tafiya dayake yawan yi sun hadu kenan sai mutuwa insha Allah, Kallan Sayyid dake cin abinci yayi a natse yana kallan Ummitah yaji zuciyarsa na sake karban Sayyid din cikeda Kauna sbd Aurensa dayake kan Ummitah bazai rabasa da ita ba tinda shi kansa mahaifinsa a hannunsa ya basa amanarsa kuma ya karba har Abada insha Allah. Yanzu ne yakejin Nutsuwa da godewa Allah da hakan dan Sayyid dinne kadai Ummitah zata aura suci gaba da zama a taredashi, Ahankali ya bude bakinsa cikin sauti me nutsuwa da rashin sauti yace "Thank you Sayyid" Kallansa sukai dukkaninsu dukda ba sauti yayi maganar cikin turancinsa dayake kashe Sayyid. Mama ce kadai da batasan wani thank you ba bata kallesa ba. Bai wani ci abincin ba hankalinsa na kan Ummitah wadda ita kuma idan yana tareda ita take cin abincin dama bata saba cin ba sbd jin take komai nata ya bude. Mama tasan daman indai yana tareda Ummitah ba wani abincin kirki yake ci ba dan haka bayan Ummitan ta gama sai ta kallesa cikin kulawa tace shima yaci abincin. Tea da chips mara maiqo yaci yana gamawa gaba dayansu suka miqe suka bar dining din. A shirye yake sbd yasan da kai Ummitah asibitin dan haka ma ya fito da wuri da sai yakai guraren 11 bai fitoba. Key din mota da wayarsa ya fito dasu a hannunsa sai tsadaddiyar Hular fcap ta fendi daya sako ya fito. Daga shi sai Ummitah din suka fita sai sayyid mama a gida suka barta yace ta koma bacci ta huta. Shine yake driving a hankali Sayyid na zaune a gaba sai Ummitah din dake baya tana kallan garin cikeda shaawa da burgewa. Sayyid dayake yana fitowa sosai suna tafiya gurare daman can sai baya wani kalle kalle sosai sbd ya saba ganin ire iren hakan. Wani babban private clinic me tsada sosai yakaita suna isa babu wani jira ko bata time a asibitin sbd kyanta akai mata registern Prenatal visit da zata ringa zuwa. Wani Dr Ken ne ya dubata dakyau cikeda kulawa ganin Yanda ABDULAZIZ sam tsananin kaunarsa akanta bata boyuwa duk da bai saniba ko shine mijinta ko yayanta koma waye a gunta kaunarsa a bayyane take. Scanning akai mata bayan angama diban jininta da sauran samples na aune aune da zaa mata. Cikin kulawa da sake fuska sosai yana tayasu murna ya kalli ABDULAZIZ daya dawo dakin bayan angama Scanning din yace "Congratulations Sir its a baby girl" Kallan Tvn yayi Ahankali kafin ya dawo da kallansa kan Ummitan da itama shi ta kalla suka kalli Sayyid a tare wanda farin cikinsa shima yake a fili sedai a duk lokacinda ABDULAZIZ yake kusa baya zaqewa akan Ummitah dama cikinsa dayake jikinta sbd kawaici da nauyin ABDULAZIZ din. "Thank you dr" Yafada yana karban result din suka fito yana rasa yanayin dayake ji a zuciyarsa duk da abu daya ya sani shine kome Ummitah zata haifa ya fito a cikinta,jininta zai kaunacesa kaman yanda yake tsananin kaunarta. Sun dade a asibitin sbd formalities din da daukan time da kuma aune aunen, Suna baro asibitin kai tsaye shopping mall ya biya dasu aka siya fruits masu yawan gaske suka wuto gida sbd bayason yayi yawo da Ummitan dan yanayinta. Suna isowa gida barwa Sayyid ita yayi ya wuce bangarensa dan Amsa waya da kuma fitowa sallah dan time yayi na laasar sunyi azahar already acan. Dakin Mama suka nufa sayyid da Ummitan. Zaunawa tayi gefen mama tana dan kwantawa jikin maman tana cewa "Mama harna dan gaji" Murmushi mama tayi tana shafa fuskanta da kulawa tace "Ummitan Mama Allah dai ya nunamun kin haihu lafiya dan ki samu hutawa kema" Murmushi tayi tana dafa cikin sbd motsawa da yayi tana cewa "Amin Mamana" Sayyid zainawa yayi yana fadawa maman duk abinda akai dama abinda dr yace cewan mace ce "Kai jamaa har yasan abinda zaa haifa kenan shi likitan" Dariya sayyid yayi yana cewa "Ba gashi mun saniba kuma nasan Shima hamman daya sani yasan 'ya zai samu irin Ummitah ba namiji ba dan bansan tayaya zai sake dashi ba amma macen ita ya saba yasan yanda zai tarairayeta kamar mamanta da haryanzu taqi sanin ta girma" Harararsa Ummitah tayi tana sake kwantawa jikin maman tace "Maman Ummitah kina jinsa dai ko? Yanzu ina cewa zan fadawa hamma zai fara kama kansa amma ita mama ka renata kana fada mata hakan" Dariya yayi yana daukan ruwan sanyin da Fiddausi ta kawo ta ajiye musu ya bude yasha yana cewa "Mama kinji zata lauye zance na ko?? Dariya maman tayi tana cewa "Ai ku duka indai hakan ne kun renani sam bakwa jin kunyata ko kadan" "Mama shine dai bayaji tinda shine sirikinki nikuma ai bazanji kunyan mamana ba" Katseta yayi da cewa "Nima ai Maman tawa ce shiyasa banajin kunyarta" Dariya maman take musu tana cewa "To ya isa naji ni na hakura tinda babu wanda yakejin kunyar tawa a cikinku Nima kuma banason aji kunyar tawa tinda maman taku ce kaman yanda kuka fad" Bata fuska Ummitah tayi tana sake hararsa tana cewa "Gaskia Ni mama saiyaji kunyar mamana tinda a gidansu inajin kunya sosai fa" Dariya yake mata datake qarawa Kyakkyawan fuskansa shima kyan ganin yace "Bafa zaki sakani jin kunyar mamana ba tinda dai nima na zama dan gaban goshinta nama kusa kamoki" Tashi tayi daga jikin maman tana kallanta zatai magana maman ta katseta da cewa "Kyalesa fada yake dan kiyita fitinar rashin dalili, Banda kamarki a rayuwata kinji Ummitan mama" Murmushin jin dadi tai tana harararsa shima dariyar yake mata. Miqewa yayi yana ficewa sbd sallah da ake kira. Bedroom dinsa ya nufa ya shiga toilet yayi alwala ya fito daidai ABDULAZIZ ya fito cikin wasu kayan daban ba wanda suka dawo dashi ba a jikinsa suka nufi masallacin tare yana tambayarsa yayiwa mama bayanin yanda Ummitah zata ring shan maganinta koda baya nan. Eh ya fada masa suna isa masallacin dayake estate din nasu. Suna dawowa daga masallaci abinci sukaci tareda shi da Ummitah da sayyid sedai Fiddausi ta kawo fruits da aka gyara wanda shi sune best abin shansa dan haka Ummitah ma su ya sakata sha sosai bayan taci abinci. Suna gamawa palonsa ta bisa acan suka zauna shida ita yana wayoyinsa da fira da ita da biyewa zantukanta. Sai magrib suka suka fito ya tafi masallaci ita kuma taje daki tayi sallah Sayyid baya nan sai da akai sallan ishai suka dawo gidan shida Hamman. A palo suka zauna su dukansu suna fira da mama wadda taketa biyewa Ummitah sa sayyid yake sakowa gaba da tsokana amma yana dan kaucewa sbd Hamman dayake gurin. Hamman yana lure dasu da yanda sayyid ke tsokanarta sai ya dan dauke kai yana fira da mama sbd kada ya takurasu. Sunci abincin dare banda shi sbd baya buqatan cin wani abincin tinda da yamma sukaci lunch energy drink kawai yasha yayi wanka yayi shirin bacci ya kwanta. Ummitah sayyid ne ya bata Maganinta bayan tayi shirin bacci tukuna suka kwanta a dakinsa. #MAMUH #HOTLOVE #ROMANCE #CRAZYLOVE #THE GREAT AZIZ AY LIMBA #JANNAH DZAD ZAADEN *_Arewabooks@Mamuhgee_* 21 *ZUZEAM VENTURES* Best APHRODISIAC 08144015291 Aslm barkanmu da wannan lokaci Ina Mai farin cikin sanar daku cewa Zuzeam ventures takawo maku ingantattun magunguna masu inganci cikin Aminci Muna da kaya kamar haka Mallaka Maganin sanyi Maganin cire tumbiMaganin farin jini Maganin matsiMaganin mata Maganin sa ni’ima da dandano Dulka Amare Set na gyran jiki Set na amarya Tabaje tsumin Gomba Xuma kiba ta hips and Brest Magungunan gyran Brest Magungunan Karin hips Maganin sliming Muna da kaya masu inganci cikin sauki da rahusa Ina wadda keneman mallaka sahihiya quaranty wlh hajiya kixo ga zuzeam ventures xakiji ddin mallaka duk fadin ran ogah duk fadansa wlh sai yyi sanyi 08144015291 Idan maganin mata kikeso akwai Idan gyran jiki kikeso gyran fata gyran Brest magungunan sa kiba da hips DOMIN samunta Kai tsaye kira wannan no 08144015291 DOMIN mgn da ita whatapp 08144015291muna tura kayanmu ko ina cikin iKon allah 🥰👌🏻 Bononza Bononza Tsimin mangoro 1k🥭 Tsimin dabino 1k Gumba ukku balai 700 Gumba aya da nonon rakumi 700 Garin kafi ciccibi 500 Garin bata gaban kishiya 500 Matsin mallaka tada zaune tsaye 2500 Turaren mallaka ba aba mai kishiya 2500 Total kayan 9500 Za a bakisu akan 3800 Kuma mutun goman farko nadakyautar Abun 2k 🗣️🗣️🗣️🗣️🗣️🗣️ ASSALAMU ALAIKUM ALHAMDULILLAH YAN UWA NEW PROMO YA KAMMALA💃🏽💃🏽💃🏽😁😁😁 da 5k dinki ki kwashi kayan 12k hajiyata 💃🏽💃🏽💃🏽😃🙃Kazar gadali ta mallara Rabi 3500 Tsimin gam gam 1500 Ruwan kara zunzurutun dadı😋800 Garin 7in1 1k Gumba 3 balai 500 Gumba kwakwa da dabino 500 Infection ruwan tsarki 1k Garin zunzurutun dadi 1200 Matsin ba a fira d wando 500 Matsin infection mai matse mace gam 500 12k All at 5k kedai dannan link dinnan don samun naki ki maza kiyi bucking koda kudinki saida Rabonki *********** Washe gari breakfast kawai suka gama su anty maryam suka iso gidan da yara gaba daya nan mama da Ummitah sukai murnan zuwansu. Sai guraren 11 ya fito suka gaisa da anty maryam da yaran tukuna ya fice gidan tareda sayyid. A gidan su anty maryam suka wuni har dare tukuna suka tafi sai alokacin ya samu ganin Ummitan da kyau tana palonsa har bacci ya fara daukanta kafin suka rabu. Washe gari ma fita yayi da Sayyid wansa yake kokarin sakawa a jikinsa sa huldodinsa duk da karatun zaiyi amma yana buqatan ya sakasa a business dinsa tinda shekarun Sayyid din sun wuce a ce sai yanzu ne zai fara university. Mama da Ummitah kwata kwata basu samu kansu a cikin wani kadaici ko damuwa da kewan gida ba sbd ABDULAZIZ shine farin ciki da abinda suke buqata a rayuwarsu to tinda suna tareda shi babu wani abu dasuke buqata ko kewa sbd ya maye gurbin duk wani abu da rayuwarsu take buqata, Inda yake shine inda suke buqatar kasancewa kuma a dik inda yake acan farin cikinsu yake so babu komai a yanzu rayuwarsu bayan kwanciyar hankali da farin ciki tareda nutsuwa. Sayyid ma yanda ABDULAZIZ LIMBA yake jansa a jikinsa cikin Rashin damuwa da rashin saninsa akan wasu abubuwan yana kokarin sauya masa rayuwa a lokaci mara tsayi ya sakasa yake sake jin matsayinsa yana wuce sirikinsa yana jinsa tamkar dan uwansa na jini tamkar yayan da suka fito jini daya dan haka ya bude kansa sosai dan fahimtar komai ya zama wanda ABDULAZIZ LIMBA zaiyi alfahari dashi. ******Rayuwa ta sauyawa su Ummitah,umma da sayyid harma dashi ABDULAZIZ din dayake tareda familynsa yanzu, Rayuwa tayi dadi ta samu kwanciyar hankali da nutsuwa sbd suna tareda junansa a cikin arzikin da Allah yake sake bude masa tareda matsayinsa dake qara yin sama hakama ya zama abokin manya dan abokan huldansa na nan din duk manyan mutane ne, Jin dadi da daula babu abinda bai wadata fmlynsa dasu ba, Babu abinda suka nema suka rasa, Rayuwa suke ta tsari da farin ciki, Tsananin kaunar dake tsakaninsa da hasken idaniyarsa ya qaru baya boyewan da Familyn Alh Saad suke mamakin irin wannan kaunar da shaquwar da basu taba gani ba sbd basu taba ganin abinda ABDULAZIZ LIMBA baya wasa ko kadan dashi ba yake bawa mahimmanci fiyeda kansa da rayuwarsa kamar Ummitah da abinda yake cikinta, Bayan Ummitah a rayuwarsa mama itace mutum ta biyu da bai hada da komaiba amma ita kanta maman tasan Ummitah itace rayuwarsa da har take tausayinsu duk ranar da Allah ya dauki daya a cikinsu yabar dayan. Duk ta tino akwai ranar hakan ko bayan sun tsufa sai taji hawaye na cika mata ido tsoro na kamata dan kuwa koda bata duniyar ita alokacin tasan Allah ne kadai zai hana wanda aka bari zarewa. Fatanta Allah ya saukakawa kowannensu kaddarar da Allah ya rubuto musu ya zama gata ya basu kariya daga sharrin duk sharrin dayake duniyar. A rayuwarta bata da adduar tin daga ranar da suka dawo hannunta sai tasu, Uwa da ubanta kadai takewa addua sai ABDULAZIZ da Ummitah sbd mantawa takeyi ma da ba itace ta haifesu ba sbd kaunarta akansu ta gaskia da tsafta ce. Cikin Ummitah yanata sake kusantar watannin haihuwarsa cikin Aminci da lafiya dan ta dena yawan ciwukan datake ta fama dasu wanda yawancinsu damuwace dake cin zuciyarta akan rashin 'dan uwanta. ABDULAZIZ LIMBA duk tarin ayyuka da schedules dake gabansa basa hanasa bawa Ummitah kulawan datake buqata daga garesa dan kuwa bai taba hada hidimarta da komaiba, Kowanne dare tana tareda shi sai lokacin baccinta yayi ta tafi dakin mijinta tayi kwanciyarta, Kulawan dayake bata daban take da kowa a gida, Su mama ma basa hanasa sosai aka basa damar kulawa da yar uwarsa yanda ya kamata, Duk ranar zuwa awonta shine da kansa yake ture ayyukan gabansa yakaita da kansa a dubata y dawo da ita. Siyayyar haihuwarta aka fara wadda yake yinta kamar ba baby daya zata haifa ba, Duk baqin ciki da quncin dayake a zuciyarsa na rashin da suke ciki a alokacin da aka haifi Ummitah da yanda suka ringa yawo da ita batada suturar sakawa a kan cikin Ummitah ya rage radadinsa dan kuwa bazai taba mantawa da hakanba har abada, Bayan irin wadda yakeyi haka ya saka Anty maryam daukansu Mama da Ummitan sika ringa fita siyayyar haihuwan. Kaman yanda mama batada adduar daya wuce nemawa rayuwar ABDULAZIZ din albarka itama Ummitah batasan uwarta batasan ubanta sai ABDULAZIZ wanda yake uwa da ubanta dan haka adduarta koyaushe akansa ne sai mama da sayyid wanda shima tasa kaddarar tazo a cikinsu dan shima kauna me karfi da tsafta yake musu. Sun fara sabawa sosai da abujan sbd famlyn gidan Alh Saad da suka zama tamkar family daya dasu kuma koyaushe suna tare da anata hayaniyar datake saka ABDULAZIZ sakewa Anty maryam da yaranta kudi sosai sbd suna saka familynsa farin ciki da walwalwa babu wani ji da kai, Shi kuwa duk wanda zai saka Ummitah da mama dariya da farin ciki babu abinda bazai iya masa ba dan haka itama anty maryam dataga hanyar cin arzikinta tazo sai bata tsaya cutar da kanta da girman kai ba ta zage tana nuna musu kauna da kulawa harma da yawo datake daukansu suna fita harsai da ABDULAZIZ din ya dan taqaita musu sbd Ummitah bayason tana yawaita yawon sbd yanayin. Dr ken ta nasa bangaren ya dage da kulawa da Ummitah wadda results dinta ya sakasa yin wasu test akanta da sunan checkup sbd bincikensu akanta daya nuna komai nata lafiya kalau da kuma bgroup nata da sauransu. Shekarunta dasuke kusan daidai dana wanda ake nema yake sake sakasa jin son tsananta bincikensa akan lafiyarta duk da a dayan bangaren tsoro ne me tsananin gaske yake cikasa akan hakanan sbd ABDULAZIZ da har yanzu baisan alaqarsa da ita ba kuma alamu suna nuna shima kila zai iya kisan akanta kaman yanda ake neman rayukan akan wadda akeson bawa new life suma. Numfashi ya sauke a lokacinda dukkanin sakamakon full binciken da yayiwa lafiyar Ummitah wadda kusan 99% sun samu abinda ake buqata, Baima taba samun matching kamar hakan ba wanda komai yayi fiyeda ma abinda ake buqata. Numfashi me zafin gaske ya sake saukewa a karo na babu adadi yana jin zuciyarsa na shiga tsoron aikata abinda yake son aikatawan sedai kuma Alkhairan da burikansa da zaa cike masa harma fiyeda yanda yake burin na son barin qasar zuwa uk dan fadada karatunsa tareda iyalansa cikin wadata ya sakasa jin kuma zai iya aikatawa. Dafe goshinsa yayi yana sauke ajiyar zuciya me karfi, Hada takardun yayi tareda sakasu a folder qarama ya saka a envelope yayi sealing tareda tattara wayoyinsa da laptop dinsa ya miqe ya nufi kofa ya fita office dinsa ya rufe ya nufi parking lot inda motarsa take ya bude ya shiga ya tada yaja yabar asibitin yana fidda wayarsa dan kiran wanda zai miqawa takardun dan baisan Asalin su waye suke buqatan heart transplant dinba dan kuwa duk wainda aka saka aikin barnar basusan asalin su waye masu aikin ba kawai dai sun san zasu bar qasar bare ma a gane career dinsu ya lalace. Washe gari Ummitah tazo ganin likita tareda ABDULAZIZ wanda zaiyi tafiya me mahimmanci a kwanakin hakan ya saka kawai gabaki daya Ummitah ta sauya jin tsoron tafiyar tasa data samu kanta a ciki mai tsananin dayake yawan fadar mata da gaba dan haka ahankali zazzabi yake yawan shigarta. Dr ken kuwa ganin yanayin Ummitan ya sakasa jin wani irin farin ciki sbd akwai alluran dayake buqatan yi mata. Babu wani bata lokaci cikin nuna kulawa da tattali yana rarrashinta yayi mata alluran suka dawo gida. #MAMUH #BESTLOVE #ROMANCE #JANNAH ZAD *_Arewabooks@Mamuhgee_* 22 *ZUZEAM VENTURES* Best APHRODISIAC 08144015291 Aslm barkanmu da wannan lokaci Ina Mai farin cikin sanar daku cewa Zuzeam ventures takawo maku ingantattun magunguna masu inganci cikin Aminci Muna da kaya kamar haka Mallaka Maganin sanyi Maganin cire tumbiMaganin farin jini Maganin matsiMaganin mata Maganin sa ni’ima da dandano Dulka Amare Set na gyran jiki Set na amarya Tabaje tsumin Gomba Xuma kiba ta hips and Brest Magungunan gyran Brest Magungunan Karin hips Maganin sliming Muna da kaya masu inganci  cikin sauki da rahusa Ina wadda keneman mallaka sahihiya quaranty wlh hajiya kixo ga zuzeam ventures xakiji ddin mallaka duk fadin ran ogah duk fadansa wlh sai yyi sanyi 08144015291 Idan maganin mata kikeso akwai Idan gyran jiki kikeso gyran fata gyran Brest magungunan sa kiba da hips DOMIN samunta Kai tsaye kira wannan no 08144015291 DOMIN mgn da ita whatapp 08144015291muna tura kayanmu ko ina cikin iKon allah 🥰👌🏻 Bononza Bononza Tsimin mangoro 1k🥭 Tsimin dabino 1k Gumba ukku balai 700 Gumba aya da nonon rakumi 700 Garin kafi ciccibi 500 Garin bata gaban kishiya 500 Matsin mallaka tada zaune tsaye 2500 Turaren mallaka ba aba mai kishiya 2500 Total kayan 9500 Za a bakisu akan 3800 Kuma mutun goman farko nadakyautar Abun 2k 🗣️🗣️🗣️🗣️🗣️🗣️ ASSALAMU ALAIKUM ALHAMDULILLAH YAN UWA  NEW PROMO YA KAMMALA💃🏽💃🏽💃🏽😁😁😁 da 5k dinki ki kwashi kayan 12k hajiyata 💃🏽💃🏽💃🏽😃🙃Kazar gadali ta mallara Rabi 3500 Tsimin gam gam 1500 Ruwan kara zunzurutun dadı😋800 Garin 7in1 1k Gumba 3 balai 500 Gumba kwakwa da dabino 500 Infection ruwan tsarki 1k Garin zunzurutun dadi 1200 Matsin ba a fira d wando 500 Matsin infection mai matse mace gam 500 12k All at 5k kedai dannan link dinnan don samun naki ki maza kiyi bucking koda kudinki saida Rabonki ************** ABDULAZIZ tafiyar ta zamar masa dole ne dayake buqatan yi wanda zaiyi ne ya dawo a qanqanin lokaci kafin ta shiga watan haihuwanta da baifi wata daya ba dan haka yayi mata alkawarin kafin lokacin zai dawo insha. Shiru tayi ahankali a lokacinda ya gama fada mata hakan yana kallanta da fararen idanuwansa da suka sauya sbd yanayinta, "Fatima"  ya ambaci sunanta cikin nutsuwa da sauti mara karfi cikeda sanyi. Kasa dagowa tayi sai wasu irin hawaye masu dumi suka gangaro ahankali kan fuskanta tanaji bugun zuciyarta na bugawa sosai. Handkerchief ya ciro daga aljihunsa ash yana qamshi ya dago fuskanta da hannunsa daya yana goge mata batateda ya iya cewa komaiba. Jin tayi wani irin abu yana taso mata mai radadin data rasa sanin menene ta fasa wani irin kuka mara sauti da ciwo tana qanqame hannunsa dayake riqe da fuskanta. Ja Idanuwansa sukai take zuciyarsa na cikewa da wani irin dacin da shima baisan daga ina yake sauko masa ba, Kukanta ne yake ratsasa yana rusa duk wani sanyi da kuzarin dayake rayuwarsa gaba dayanta, Ahankali daqyar ya iya furta sunanta na asali wato Fatima a karo na biyu sedai ya kasa cewa komai kukanta ne kawai ke ratsa kunnuwansa yana rusa kuzarinsa. Wani irin nauyi da radadi takeji a zuciyarta na rabuwa dashi wanda bata taba jinsaba a rayuwarta amma bazata iya fada masa hakan ba sbd tana fada komai alkhairi da cigaban da zai samu a tafiyar zai iya fasawa akan hakan dan haka ta dago idanuwanta da sukai jajir ta kallesa tana taqaita kukanta dan ganin yanayinsa kuma ta san ba komai zai iya cewaba. Ajiyar zuciya me sanyi ta sauke tana kallan idanuwansa da sukai jajir ya zuba mata su baice komaiba, Ahankali ta sake murmushin karfin hali daya bayyanarda kamarsu sosai kaman an tsaga kara ta bude baki tace "Hamman Ummitah Allah ya tsareka idan ka tafi ya baku dukkanin Alkhairin dayake cikin wannan duniyar da tafiyar" Numfashi ya sauke mara sauti kalamanta na dukan zuciyarsa ya dan rintse idanuwansa ahankali ya bude ya bude baki da nannauyan sauti mara hayaniya yace "Bakyason na tafi saikin haihu right?? Zuba masa idanuwanta tayi tana kallon Asalin kyau da haibar da Allah yayi masa wanda tasan duk macen da Allah yayi itace matarsa tayi dacen namijin da duk wannan kyan halittar tas zuciyarsa tafi kyau da tsafta. Girgiza kai tayi ahankali tana riqe hannunsa cikin nata dakyau ta sanyin murya me nutsuwa tace "Aa,ka tafi ina jiran dawowanka insha Allah kafin na haihu... Numfashi ta sauke me sanyin daya sakasa kallanta ta dago da sanyi muryanta na fitowa a tausashe tace "Hammah ka dawo da wuri sbd inason na haihu kana nan, Inason kafara daukan abinda zan haifa kaman yanda kaine kafara daukana dana taho duniya.. Shiru yayi yana tino rayuwar azaba da gararin dasukai shida mahaifiyarsa a lokacin renon cikin Ummitah.... Wani irin nauyi da daci kirjinsa ya cikeda dashi jikinsa na mutuwa yana kasa kallan Ummitan data zuba masa ido tana karanto dacin dayake cike zuciyarsa idanuwanta suka ciko da hawayen da suka gangaro gefen idonta. Ranar haihuwarta ya tina irin ukuba da qangin da mahaifiyarsa ta shiga tareda juyewan hankalinta tareda gararin datai cikin rashin hankali har bacewanta... Hawayenda tin lokacin batar mahaifiyarsa bai sake sanin ya ake zubdasu ba sbd taurin zuciyar dayake dashi ne suka ciko Kyawawan idanuwansa ya rintse idanuwan yana hadiyesu dan radadin Rashin mahaifiyarsa shine radadi mafi munin dayake yanka zuciyarsa. Ahankali Ummitah ta kwantar da kanta kafadarsa tana kasa cewa komai sai hawayen da suke gangaro mata tana son ta tambayesa kamannin Mahaifiyarsu da mahaifinsu da bata taba saniba sedai tanajin radadin dayake ji na tinano ranakun quncinsu na baya da suka wuce dan haka bata iya cewa komaiba shiru kawai sukai babu wanda yace komai har kusan dare sosai ta tashi yakaita har dakinta ya kamo hannunta ya saka mata wani tsohon hoton daya tsufa sbd har ruwan sama yasha sosai sbd wahala ya juya ahankali ya wuce bedroom dinsa. Zaunawa tayi a sanyaye bakin gadon dakinta tareda dago hannunta da yayi mata sanyi ta bude hoton ta zuba masa idanuwanta da suka sauya sbd kukan datai sosai. Hoton Mahaifinsu ne tareda Hamman yana qarami sanye da uniform din makaranta a ranar daya fara kaisa makaranta a ranar sukai hoton a makarantar me hoto yayi musu shi Murmushi baban yakeyi fuskansa a sake sosai yan riqe da hannun ABDULAZIZ din shima Murmushin yakeyi na farin cikin zuwansa makaranta. Wani irin abu takejin yana tasowa a kirjinta me nauyin gaske tsananin son Mahaifinsu na mamaye zuciyarta kuka mara sauti ya taso mata ta silale a gurin tanayi tana jin tausayin Hammanta wanda ya rasa uwa da uba dan ita kam shine uwa da ubanta. Sayyid ne ya shigo dakin gabaki daya gidan a sanyaye kowa yake ba walwala sbd Ummitah gaba daya ta sauy kwana biyun bata cikin walwala musamman da tafiyar Hamman gobe ce sai gaba daya yau ta rikice bata jin dadin komai hakama suma duk sun shiga damuwa. Ko kadan a daren Ummitah bata rintsa ba hakama ABDULAZIZ din kwana yayi yana mata adduar Allah ya saukar da ita lafiya. Da asuba koda ya dawo sallah wanka kawai yayi ya shirya ya fito dan 7 jirginsa zai tashi, Sanye da Black UGG knit top da Straight jeans ya fito sai fcap ta balenciaga yana qamshi me sanyi ya fito Sayyid tini yakai kayansa mota ya dawo. Fuskansa tayi wani irin fresh yayi fayau sbd rashin rintsawar da baiyiba da damuwar datake cin ransa dayake ganin tafiyar da zaiyi ne yabar Ummitah a wannan halin. Cikin dauriya da danne damuwar ta harma da ciwon datakeji ta fito itama fuskanta tayi fayau ta qarasa har gabansa ta miqa masa hannu tana sakin murmushi me kyau dan kwantar masa da hankali. Ajiyar zuciya a fili ya sake ahankali yana mata kallan tsafta ya miqa hannu ya kama hannunta data basa sukai musabaha ta sauke ajiyar zuciya tana sake qanqame hannunsa cikin nata tace "ALLAH ya baka nasara akan abinda zakaje ya baka nasara a duk abinda zaka nema a duniya ya kuma dafa maka ya hanaka damuwa kowace iri ce... Shiru ta dan yi kafin tace "Allah kuma ya dawo da kai lafiya Hammah" "Amin ya furta ahankali yana kallan cikin idanuwanta da ita shi take kalla tana murmushi me kyau da nutsuwa. Mama ya kalla da sayyid yace "Idan akwai abinda ya taso a kula sosai a tafi asibiti akirani,a kula" Addua mama tai masa itama tana masa fatan dawowa lfy. Hoton daya bata jiyan Ummitah ta fidda   a cikin dayan hannunta ta saka masa shima a hannunsa tana cewa "Nagode Hammah" Murmushin karfin hali shima yayi mata yana shafa fuskanta ya matso kaman yanda ya saba ya karanta mata adduar dayake mata tin tana yarinya ta neman tsarin ubangijin a kunnenta ya share mata hawayen da suka gangaro mata tana murmushi ya juya ya shige mota yana daga musu hannu. Sayyid ne ya shiga motar sbd tareda shi zasu Airport din da drivern gidan Alh Saad. Motarsu na barin gidan gidan ta sauke ajiyan zuciya me karfi tana jin wani abu kamar yabar jikinta dan haka mama ta jata suka koma cikin gida. Koda Sayyid ya dawo daga Airport bai dameta ba kyaleta kowa yayi sbd ta samu ta warware da kanta sedai hakan bai yiyiba dan kuwa zazzabi me qarfine ya kamata wanda ya sakasu damuwa. Haka suka wuni da ita har dare batajin dadi sedai tace ba buqatan zuwa asibitin dan haka sai baa takurataba. Washe gari ma haka ta wuni cikin yanayi na rashin lafiyar datake cinta a hankali, Fama su mama suka fara da ita sbd gabaki daya lafiyar tana neman gagaranta sbd wani irin silent ciwo take fama dashi wanda ta rasa menene yake damunta itama hakama da kanta ta hana a sanar da Hamman sbd kada ya shiga damuwa tace zata iya daurewa har lokacin haihuwanta ya qara yi tinda ta kusa. ******ciwon kwana daya kwana biyu zai qara gaba yakeyi cikin tsananin azabar da bata taba saniba take a yanzu hakama batasan me zatace yana damunta ba ga damuwar datake damun zuciyarta da kwata kwata bata mata dadi, Wata irin rama me muni ta fara da wani irin haske dayake bawa mama da sayyid tsoro sosai hankalinsu ya tashi sosai kuma har lokacin sun kasa fadawa ABDULAZIZ din. Zuwansu asibiti biyu dr yana dubat yana ce musu lafiyarta kalau kawai yanayi ne na haihuwan daya matso. Dawowa sukai gida suna cigaba da kulawa da ita sedai tashin hankalinsu da tsoronsu tsananta yakeyi sbd qarewa takeyi kamar wadda mayu suka kama takai komai tafara gaza yiwa kanta jinya takeyi sosai wanda ya fara taba lafiyar cikinta. Dole suka tattara suka sake komawa asibiti gashi anty maryam bata nan su kadai suketa Fama sai drivern da aka samar musu sbd fitarsu. ********Dzad ne a zaune a lafiyayyar office dinsa dayake cikim mansion dinsu ya zare farin glass dinsa yana kallan Ammar wanda Maheer ma shi yake kalla. Numfashi Ammar din ya sauke cikin samun nutsuwar biyan buqatan shekara da shekaru yace "Komai na matar da aka samu zuciyarta ya kammala magani ya gama aiki akanta wanda kowane time a wannan stage din datake shine daidai lokacin da zataiwa Jannah donor, Anyi bincike akanta ba kowa bace daga kauye suka taho suna zama gidan wani relative dinsu ne wanda baima cika zamaba so bandai tsaya nasan sunansa ba kokuma buqatan hotonsa sbd ba buqatan hakan, Abu daya ne shine lokaci yayi zuwa jibi zaayi aikin wanda muke fatan wannan shine na karshe sbd baa taba samun matching din da ake tinanin yayi 99% ba kuma gashi cikin ya riga yazo lokacin haihuwa so the right and perfect time has come" Maheer jin yayi wani nauyi da sanyi na cike zuciyarsa lokaci daya Dad ma jin yayi bayajin komai baya buqatan komai kawai ayi aikin su samu abinda suke so shine burinsu. Nutsuwa da nauyin daya danne musu zuciya shekara da shekaru ne sukaji dukkaninsu yana fada musu. Washe gari ranar da zaayi aikin Anny ce ta bawa Jannah maganin data yanke jiki aka kwasheta zuwa asibitin sbd suna buqatan ta kasance a asibitin koda zaa shigo da Fatima Abdulaziz Ayoub din Wannan shine sunan dayake jikin katinta. Ummitah kuwa a daren ranar gabaki daya jikinta ya rikice jini ne yake mata zuba ba kakkautawan daya saka a cikin daren mama da sayyid suka kwasheta zuwa asibiti hankali tashe. Dr ken yana asibitin daman yana jiran zuwansu sbd yasan hakan zata faru, Dayake ansan shine dr dinta kiransa akai da gaggawa A rikice cikeda kulawa da tashin hankali yayi kanta yana kiran nurses. Naquda ce ya tayar mata tareda mata allurar da zata hanata iya haihuwa da kanta dan haka hankalin nurses ya tashi gashi bleeding takeyi sosai gashi tayi wani irin ciwon data jima acikinsa ya bayyana sosai a jikinta. A cikin daren ganin an kasa shawo kan matsalar take yayi mata transfer zuwa ZADEEN HEALTH CEN. Su mama da sayyid tinda suka gwada kiran Hamman baa samesa ba sai suka maida hankali kan Jikin Ummitan da aka tabbatar musu ba sauki gashi private hospital ce babu mutane sosai sbd tsadarta da tsarinta. Dr ken kallansu yayi cikin nuna damuwa da kokarinsa yace "Haihuwace tazo mata gadan gadan gashi lokacin bai qarasa yiba sbd bata bude ba gashi kuma babyn ruwan dayake rayuwa a cikinsa cikin cikinnata ya tsiyaye dole Aiki zaa mata a cire babyn idan ba hakanba komai zai iya faruwa da ita har babyn dan haka aikin Gaggawa zaa shiga da ita a acikin daren nan anan likitocinmu duka basa nan Nayi muku transfer zuwa qwararriyar asibitin da muke da ita Kusa yanzu can zaa tafi da ita. Babu abinda mama da sayyid ke nanatawa bayan sunan Allah cikin matsanancin tashin hankali dan haka basuda zabin daya wuce aminta da hakan. Cikin ambulance da gaggawa akai Asibitin da ita koda suka isa tafara nisa dan haka Hannu kawai sayyid ya saka a takardun komai aka shige tiyata da ita suna kallonta kowannensu idanuwansa na cikowa da hawayen dake zana radadi a zukatansu har aka shige da ita aka rufo kofar wadda ta saka kirjin mama bugawa da wani irin ciwon daya sakata dafa bango tana silalewa qasa ta zauna har lokacin kirjinta na qara ciwo. Sayyid kuwa sunkuyar da kansa yayi yanajin kaman kunnuwansa da kansa iska na musu yawa. #MAMUH ZAFAFA BIYAR KALBIM 500 mamuhgee A DUNIYATA 500 Huguma AJIYA A DUHU 500 Billyn Abdul KIRJIN ME HANKALI 500 Miss xoxo Pay at 0022419171 AccessBank Maryam sani gummi Shedan biya 09033181070 Or mtn vtu at 09032345899 *_Arewabooks@Mamuhgee_* 23 *ZUZEAM VENTURES* Best APHRODISIAC 08144015291 Aslm barkanmu da wannan lokaci Ina Mai farin cikin sanar daku cewa Zuzeam ventures takawo maku ingantattun magunguna masu inganci cikin Aminci Muna da kaya kamar haka Mallaka Maganin sanyi Maganin cire tumbiMaganin farin jini Maganin matsiMaganin mata Maganin sa ni’ima da dandano Dulka Amare Set na gyran jiki Set na amarya Tabaje tsumin Gomba Xuma kiba ta hips and Brest Magungunan gyran Brest Magungunan Karin hips Maganin sliming Muna da kaya masu inganci cikin sauki da rahusa Ina wadda keneman mallaka sahihiya quaranty wlh hajiya kixo ga zuzeam ventures xakiji ddin mallaka duk fadin ran ogah duk fadansa wlh sai yyi sanyi 08144015291 Idan maganin mata kikeso akwai Idan gyran jiki kikeso gyran fata gyran Brest magungunan sa kiba da hips DOMIN samunta Kai tsaye kira wannan no 08144015291 DOMIN mgn da ita whatapp 08144015291muna tura kayanmu ko ina cikin iKon allah 🥰👌🏻 Bononza Bononza Tsimin mangoro 1k🥭 Tsimin dabino 1k Gumba ukku balai 700 Gumba aya da nonon rakumi 700 Garin kafi ciccibi 500 Garin bata gaban kishiya 500 Matsin mallaka tada zaune tsaye 2500 Turaren mallaka ba aba mai kishiya 2500 Total kayan 9500 Za a bakisu akan 3800 Kuma mutun goman farko nadakyautar Abun 2k 🗣️🗣️🗣️🗣️🗣️🗣️ ASSALAMU ALAIKUM ALHAMDULILLAH YAN UWA NEW PROMO YA KAMMALA💃🏽💃🏽💃🏽😁😁😁 da 5k dinki ki kwashi kayan 12k hajiyata 💃🏽💃🏽💃🏽😃🙃Kazar gadali ta mallara Rabi 3500 Tsimin gam gam 1500 Ruwan kara zunzurutun dadı😋800 Garin 7in1 1k Gumba 3 balai 500 Gumba kwakwa da dabino 500 Infection ruwan tsarki 1k Garin zunzurutun dadi 1200 Matsin ba a fira d wando 500 Matsin infection mai matse mace gam 500 12k All at 5k kedai dannan link dinnan don samun naki ki maza kiyi bucking koda kudinki saida Rabonki ************* Wayar hannun sayyid da yayiwa wani irin riqon dayake gap da saka screen din lalacewa batareda ya saniba sbd damketa yayi zuciyarsa najin kamar zata baro kirjinsa sbd abinda yakeji, Ummitah bayan mahaifinsa a duniya itace abinda yakeso fiyeda komai da kansa sbd baida mahaifiya shima ta rasu, Ummitah itace wadda baya kaunar gani ko yanayinta kadai ya sauya dako ciwon kai bare damuwa ko wani babban abin, Ayau gata a gabansu anshiga aiki da ita yankata zaayi a ciro abinda yake cikin amma basuda abin yi sbd Allah yin Allah ne da ikonsa. Hawaye ne sika cika idanuwansa da sukai jajir amma sun kasa saukowa, Wayarsa ya kurawa ido yana sake saka kiran Hamman a karo na babu adadi ayau din amma har lokacin bata shiga. Cigaba yayi da kiransa idanuwansa ko gani basayi sosai hakama hankalinsa da zuciyarsa duk basa aiki daidai kawai hamman yakeson ji dan haka ya kasa dena kira kaman mara hankali hannuwansa har rawa sukeyi. Mama kuwa kanta yana qasa soke cikin qafafunta tana jin kirjinta na tsananta nauyi dan haka ta daure cikin karfin hali tana tsananta adduarta akan ayi aikin lafiya su samu daga uwar har yar lfy. Shiru tsit gurin ya dauka kwata kwata babu motsi ko hayaniyar mutane a bangaren da ake aikin wanda guri ne na musamman a asibitin ba kowa yake zuwa ba sbd bangaren masu asibitin ne da babu wanda aka taba kawowa gurin sai wanda zaa illata. Yanda hannun sayyid ke rawa cikin tashin hankali da fita hayyaci ya kasa dena kiran Hamma kaman zararre ya saka wayar faduwa daga hannunsa ta fadi tana fashewa gurin yana kallo screen yafara wani kyaftawa yana rawa a fashe haryayi duhu gaba daya ya mutu. Rintse idanuwansa yayi yana silalewa a gurin ya zauna a qasa shima duk da akwai kujera a gurin baya buqata. Adduar mama ce datake yi cikin dagewa da rashin sanya sautinta yake fita ahankali batareda ta san da hakan ba, Rintse idanuwansa yayi dake masa radadi yana adduar shima a zuciyarsa. Babu wanda suka gani babu wanda ya fito ko yazo wucewa ya gansu zaman azabar jira kawai sike tsawon awanni ba labari. Kiran asuba ake farawa tinda daman a tsakar daren suka iso asibitin, Kiran farko da aka kwada yayi daidai da bude kofar dakin tiyatar wanda ya saka mama da sayyid din miqewa a tare suna zubawa kofar jajayen idanuwansu zuciyoyinsu na wani irin sanyin da basu iya taku ko daya ba. Dr Abraham sanye da kayan tiyata da hula ne a gaba sai dr finn a bayansa da wata Nurse wadda ba kowa bace Anny ce wadda take sanyeda face mask fari da kayanta na Nurses. Ammar ne ya fito karshe shima sanyeda facemask din na likitoci da wularsu ta tiyata akansa baiko kalli inda su maman da Sayyid sukeba ya wuce yana jin jiri da nauyi a kirjinsa na fata da tsoron dacewa a aikin da zasu shiga yanzu na jannah. Anny ma bata tsaya kallan nasu ba tabi bayan Ammar suka bar gurin zuwa wata kofar dake gurin. Wata Nurse ce ta sake fitowa dauketa baby nade a cikin farin showel me tsananin taushi da tsadar dasuka taho dashi aka karba tin acan asibitin dr ken. Tinkarosu Nurse din tayi da babyn wadda take lafe idanuwanta a rufe. Dr Abraham da dr fin sai wani likitan daya fito baqi ne bahaushe musulmi ma yana zare hular kansa ya wuto gaba yana kallansu suma akansa suka maida kallansu suna kallansu da imaninsu sbd ganin shine nasu tinda su dr Abraham turawa ne bama gane musu zasuyiba. Nurse ya kalla tana miqawa Sayyid din baby ya miqa hannuwansa cikin wani irin farin ciki dayake saka jikinsa rawa yana kokarin karba Muryan dr ismail wadda take tafe da bayayyanarda radadi da alhinin kai tsaye ta sauka a kunnuwansa.... "Anyi nasarar cire mata abinda yake cikinta cikin koshin lafiya sedai ALLAH YA KARBI RAN UWAR bawa baya wuce lokacinsa ayi haku........ Sakin jaririyar hannunsa Sayyid yayi cikin mummunan shock din dabai masan yayi hakanba. Nurse dince tayi saurin zubewa qasa ta tare babyn a hannuwanta cikin ihu. Wani mugun busashiyar yawu mama take kokarin hadiyewa amma ya kasa wucewa yankar mata maqoshi tanaji yanayi kaman da wuqa dan haka ta kyafta idanuwanta da suka qanqance tana kallansu daya dayan daya kafin ta tsayar da idanuwanta akan dr ismail din da qyar ta tina bakinta zata bude ba hannuwanta datake budewa ba muryanta na yankewa tace "Kace an sauka lafiya ko? Ita Ummitan fa? Numfashi me zafin gaske ya sauke yana kallan Sayyid da yayi mutuwar tsaye yana wani vibrating amma tambayar maman ta sakasa dago jajayen idanuwansa da suke neman fashewa ya kallesa yana son jin amsar tamyar maman dan shima abinda yakeson tambaya amma ya manta yaya ake bude baki ayi magana gaba daya.. Sunkuyar da kai dr ismail din yayi yana kasa kallan idanuwansu da suka zuba masa ya bude baki yana tausasa harshensa yace "Babu yanda zamu iya dukkaninmu akan hukuncin ubangiji, Hakuri zamuyi dukkaninmu, AN RIGA AN RASATA,TA RASU ABINDA TA HAIFA KAWAI AKA SAMU....." Mama bakinsa take kalla kalaman na fitowa daga bakinsa kafin ta juya ta zubawa kofar dakin idanuwanta kafin ta sake wani yunqurin wani bugu kirjinta yayi so daya ta yanke jiki a gurin ta zube idanuwanta na juyewa gabaki daya. Sayyid kuwa baya yayi kafafunsa na kasa daukansa ya durqushe a gurin yana fasa wani irin irin ihun daya saka gabaki daya rabin asibin daukan qarar kafin ya fasa wani irin kukan daya saka su dr Abraham yin baya cikin firgita sbd kukane daya zo masa kansa na zarewa gabaki daya yana wata irin jijjigar data saka dr Ismail kasa riqe abinda yakeji ya rungumesa yana jin idanuwansa shima cikowa da hawaye sbd radadin abinda sukai dayake ji a zuciyarsa wanda yayi a bisa rashin zabin dayake dashi. Riqe sayyid din yayi a cikin jikinsa sbd irin jijjigar dayake zata iya sakasa samun collapse wanda zai iya qin tashi idan hakan ta samesa. Jijjiga me karfin gaske yakeyi yana wani irin kuka me gunjin daya saka nurses dake kusa tahowa sun kallansa cikeda wani irin tausayi me cikeda tsoro sbd ganin namiji kamarsa yana irin wannan kukan me tada hankali. Mama kuwa dr Ken ne yace nurses suyi saurin daukanta akaita emergency sbd ita kam kamar raima ya fita a jikinta. Sayyid ma rikicewa yanayinsa yayi dole cikin tsananin gaggawa dr ismail yasa akai emergency dashi sbd wani irin kumfane ma yake fita bakinsa kaman yana kokarin samun wata matsalar ne suna buqatan gaggawar dawo dashi daidai. Nurse Latifat aka bari da babynsu a hannunta tana yawo da ita sbd tashin hankali da firgicin ganin su dukan suna neman mutuwa a asibitin tasu. Dr Abraham da dr finn kuwa Bayansu Dr Ammar suka bi sbd shiga tiyatar Jannah wadda Allah yayi sun samu abinda suke zo ba matsala fatarsu daya yanzu ana sakawa tayi saurin matching da vessels na jikinta batareda tasha wahalar kafin gama sabawa ko binding na komai daga zuciyar zuwa jikinta da jininta. Duk yanda Su dr ismail da wasu likitocin suka shawo kan Sayyid kasawa sukai gashi sai muni jikinsa yakeyi dole sikai rendering nasa unconscious. Mama kuwa kaman qaramar coma ta shiga sbd komai nata dena aiki yayi. Tsit bangaren yayi babu mafitar komai har rana tai daga mama har sayyid babu wanda aka samu kansa bare asan yanda zaayi dasu ga baby ma tafara kuka sosai ga gawar Ummitah a ciki an rasa ya zaayi dasu. A wannan halin ne Baba alhassan ya iso abuja sbd tin a jiyan Sayyid ya sanar dashi jikin Ummitan aiki zaa mata dan haka jinsu shiru ya iso. Asibitin dr ken ya isa kai tsaye sbd acan ya taba zuwa dubo Ummitah wani zuwan da yayi kwanaki. Acan ana kiran dr ken da kansa yaje ya dauko Baban ya kawo Asibitin nan sbd daman neman yan uwansu suke kai tsaye. Ana kawo baba alhassan kallo daya yayiwa Sayyid yaji tasa zuciyar na neman bugawa sedai ya dauka zai iya riqewa da jarumta seda aka miqa masa baby aka sanar dashi Ummitah ta zama babu ya zube a gurin shima yana qanqame yar a jikinsa yana hada zufa me tsananin yawa da tashin hankalin dabai taba tsammanin samun kansa a ciki ba. Dr ken da dr ismail ne sukaita kokarin basa hakuri da hanasa shiga wani mummunan halin kamansu Sayyid sbd kada arasa wanda zai karbesu. Addua yayita yi yana hada zufa harya dawo hayyacinsa yana jan numfashi daqyar sbd take ciwon zuciya me qarfi ya kamasa amma ahakan ya daure yana danne azabar dayake ji a kirjinsa. Mama da sayyid din kusan a lokaci daya suka farka, Babu me karfin iya magana ko wani abu, Idanuwa kadai suke bin baba alhassan dashi wanda yake kokarin hanasu ganin halinda yake ciki ya bude baki daqyar cikin karfin hali ya ringa musu nasiha da adduar data saka Sayyid zuba masa idanuwansa suna rinewa. Mama kuwa haka suka lallaba bata iya tsayuwa da kanta baba alhassan ya saka hannu suka karbi gawarda basu saka a ido ba saida aka fito da ita a rufe aka saka musu a ambulance din asibitin dr ken wadda zata kaisu har garinsu a kyauta sbd tausayi da kuma yanda dr ken din ya nuna damuwarsa sosai akansu. Sayyid na ido biyu da gawar Ummitah rasa kansa yayi ya dafe kirjinsa dake tsananin nauyi da azababben ciwo yana kasa tafiya da kansa saida aka taimaka masa ya shiga ambulance din tareda gawar Mama da baba alhassan da baby wadda Sayyid da mama basusan yama kamanninta yake ba suka shiga motar ABDULAZIZ da drivern daya bar musu. Duk wasu takardu na tafiya da gawa an basu daga asibitin kai tsaye garin abuja suka bari ko gida basu biya ba zuwa garinsu da gawar dan acan zasuyi janazah. Mummunan tafiya ce ta qunci da dacin zuciya me tsananin gaske na mummunan rashin da sukai wanda ABDULAZIZ ma kadai da mama ke tinawa takejin kirjinta na tsananta ciwon dayake tsananta mata radadin rashin. Tinda suka hau hanya babu wanda ya bude bakinsa bare ya iya magana a cikin motarsu. Acan motar gawar kuwa Sayyid qamewa idanuwansa sukai ya zubawa gawar ido kunnuwansa na daukewa daga jin komai hakama zuciyarsa gaba daya mutuwa yakejin kaman tanayi. Gefen fuskanta dayake dan fitowa sbd iskan dayake kadawa kadan yana saka abinda aka rufeta ruf har fuska ya zubawa ido tayi wani irin haske fayau fatarta ta dan bushe kaman zata tashi tai masa magana kota ambaci sunan Hammanta. Baisan lokacinda wani irin kuka mai tsananin gaske da radadin dayakejin bazai iya riqewa ba na tasowa daga kirjinsa ya dafe kirjinsa yana durqushewa gaban gawar yanayi hannuwansa dake dafe kirjinsa suna rawa yana dukan kijrinsa sbd azabar radadin dayakeji. #MAMUH #AZIZ AY LIMBA #UMMITAH LIMBA #FALAQ LIMBA ZAFAFA BIYAR KALBIM 500 mamuhgee A DUNIYATA 500 Huguma AJIYA A DUHU 500 Billyn Abdul KIRJIN ME HANKALI 500 Miss xoxo Pay at 0022419171 AccessBank Maryam sani gummi Shedan biya 09033181070 Or mtn vtu at 09032345899*_Arewabooks@Mamuhgee_* 24 *ZUZEAM VENTURES* Best APHRODISIAC 08144015291 Aslm barkanmu da wannan lokaci Ina Mai farin cikin sanar daku cewa Zuzeam ventures takawo maku ingantattun magunguna masu inganci cikin Aminci Muna da kaya kamar haka Mallaka Maganin sanyi Maganin cire tumbiMaganin farin jini Maganin matsiMaganin mata Maganin sa ni’ima da dandano Dulka Amare Set na gyran jiki Set na amarya Tabaje tsumin Gomba Xuma kiba ta hips and Brest Magungunan gyran Brest Magungunan Karin hips Maganin sliming Muna da kaya masu inganci cikin sauki da rahusa Ina wadda keneman mallaka sahihiya quaranty wlh hajiya kixo ga zuzeam ventures xakiji ddin mallaka duk fadin ran ogah duk fadansa wlh sai yyi sanyi 08144015291 Idan maganin mata kikeso akwai Idan gyran jiki kikeso gyran fata gyran Brest magungunan sa kiba da hips DOMIN samunta Kai tsaye kira wannan no 08144015291 DOMIN mgn da ita whatapp 08144015291muna tura kayanmu ko ina cikin iKon allah 🥰👌🏻 Bononza Bononza Tsimin mangoro 1k🥭 Tsimin dabino 1k Gumba ukku balai 700 Gumba aya da nonon rakumi 700 Garin kafi ciccibi 500 Garin bata gaban kishiya 500 Matsin mallaka tada zaune tsaye 2500 Turaren mallaka ba aba mai kishiya 2500 Total kayan 9500 Za a bakisu akan 3800 Kuma mutun goman farko nadakyautar Abun 2k 🗣️🗣️🗣️🗣️🗣️🗣️ ASSALAMU ALAIKUM ALHAMDULILLAH YAN UWA NEW PROMO YA KAMMALA💃🏽💃🏽💃🏽😁😁😁 da 5k dinki ki kwashi kayan 12k hajiyata 💃🏽💃🏽💃🏽😃🙃Kazar gadali ta mallara Rabi 3500 Tsimin gam gam 1500 Ruwan kara zunzurutun dadı😋800 Garin 7in1 1k Gumba 3 balai 500 Gumba kwakwa da dabino 500 Infection ruwan tsarki 1k Garin zunzurutun dadi 1200 Matsin ba a fira d wando 500 Matsin infection mai matse mace gam 500 12k All at 5k kedai dannan link dinnan don samun naki ki maza kiyi bucking koda kudinki saida Rabonki ************* Tafiya ce me dan tsayi wadda ta sakasu isowar yamma sosai da mummunan ganin daya daga hankalin dukkanin jamaar garin sbd farin jinin Ummitah da kaunar da kowa ke mata sbd yayanta wanda duk wanda rasuwarta ta shiga kunnuwansa ABDULAZIZ ake fara tambaya sbd firgici. Tashin hankali iyalan gidan Baba alhassan da gidansu mama suka shiga me girman gaske tareda kukan da basa ma sanin ya kufce musu cikin rikicewa da tsoro me tsanani ganin gawar Ummitah. Sayyid koda suka iso baya gani kwata kwata makarantar lokaci daya ta kamasa sbd kuka da tsananin ciwon da kirjinsa yakeci mai tsananin gasken da yana buqatan ganin likita amma ba wannan damar. Mama ma riqota akai aka shiga da ita gidan baba alhassan wanda a gidan zaayi komai. A dakin Ummitah aka kwantar da maman wadda itama ganinta da jinta yake daukewa ahankali. Kasancewar yamma tayi sosai ga gawar ta jima dan haka ba bata lokaci aka fara shirin janazarta wanda Mama da Sayyid ne sukai qarfin hali da dauriyar yi mata wankan gawa da shirinta wanda mama bata gani kwata kwata sosai daurewa kawai takeyi sbd yiwa Ummitah wankan karshe da kanta. Sayyid ma hakan ne daga garesa sedai qaramin dinkin dayake kirjinta ya zubawa ido yana goge mata shi sbd baisan yaushe taji rauni a gurinba sabo hakan, Fuskanta ya dawo da idanuwansa yana fasa kukan dayake riqewa yana kasa cigaba sbd numfashinsa dayake sarkewa da sauri aka fitar dashi matar Babansa da mama ma datake kasawa suka qarasa shiryata cikin suturarta ta karshe a wannan lokacin ne zuciyar mama ta gasa itama sedai aka fiddo da ita bayan an fice da gawar Ummitah din wanda Hankalin kowa yake qarasa tashi anata kuka da firgicin tareda tsananin tausayin Dan uwanta dako gawarta Allah bai basa ikon gani ba wanda sunsani har abada bazai taba dena fita daga radadin hakan ba, Mahaifinsa ya rasu batareda yayiwa gawarsa kallan karsheba sbd babu abinda ya rage a gawar mahaifin nasa wuta ta cinye, Mahaifiyarsa ta tafiyarta tin yanada kuruciya,tana taye ko a mace bai samu ganin gawartaba itama, A yanzu ya rasa rai mafi soyuwa a rayuwarsa amma bai samu ko sassaucin ganin gawartaba. Wannan tinanin kadai yake sake saka mama da duk masu kaunarsa shiga mummunan halin dayake hana zuciyarsu samun sauki. Sayyid ana saka gawar Ummitah kabarinta yaji wani irin Nauyin daya danne kirjinsa da har abada bayajin zai sauka, Ahankali hawayen idanuwansa sukai gangarowan dayake jin duminsu har a kirjinsa da tafin hannuwansa dasuka Ummitah a kabarinta. Rufeta aka fara yanaji yana gani har aka gama rufeta akai mata addua mahaifinsa ya kama hannunsa kaman makaho yana jansa suna barin makabartan yanajin duk taku daya yana rasa ruhinsa da ganinsa sbd dishi dishin dayake gani. Suna isowa gida suka tarar da Alh saad da iyalinsa sun taho gaisuwa wanda shima yayi iya kokarinsa ne ya tarar da jana'izar amma Allah baiyiba. Tashin hankalin dayake ciki da iyalinsa su kansu bamai faduwa bane sbd ABDULAZIZ din kawai suma suke kasa tinanin ma Halinda zai shiga din gashi suna hanya kira biyu yayi masa yana cewa a aika gidansa yanason magana dasu mama sbd kaf wayoyinsu basa shiga yanata kira tin dazu. Kasa fada masa Alh saad yayi sbd yasan Komai zai iya faruwa da ABDULAZIZ din a inda baya tareda yan uwansa dan haka ya zabi boye masa saiya dawo. Mama koda ake shigowa gaisuwa da magriba bata gane kowa da komai yanda ya kamata dan haka anty maryam ta sanar da Alh saad maman na buqatan ganin likita da gaggawa fa. Daman basuda gurin kwana a gurin dan haka kwanan zaune sukai a garin ana lallabawa da mama wadda take jin kamar itama mutuwar zatai. Yanda suka ga safe haka sukaga dare a zaune cikin qunci da damuwa da ciwon rayuka. Ana gama sallar asuba Alh saad yace su shiry karfe goma na safe ayiwa Ummitan addua su tafi sbd akai mama ga likita. Mama rikicewa tayi tana cewa bazata iya barin garinba har abada sbd Ummitah na garin. Wannan kalman nata ya daga hankalinsu aka fara rarrashinta amma sam batama san tanayi ba sbd duk ta rikice kaman ta samu juyewan kai. Baba alhassan ne da kansa ya shigo ya fara bata magana yana tinatar da ita a yanzu ABDULAZIZ ne wanda ya kamata ace duk sun duqufa roqarwa Allah ya basa dangana da ikon daukan kaddara ya samu sassaucin abinda zaiji tin kafin a fada masa, Shine wanda yake tsananin buqatarta a yanzu fiyeda kowa daya rasa Ummitah sbd ita kadaice zata iya kulawa da shi idan wannan mummunan labarin ya samesa. Ambatar ABDULAZIZ kadai idan akai saitaji tana neman sake zarewa sbd kunyarsa da shakkar yanda ma zata sanar dashi Ummitah tabarsa har abada ba dawowa sedai a mafarki ko hoto amma tabbas ABDULAZIZ na buqatanta a kusa sbd duniyarsa ce zata rushe da wannan mummunan labarin. Addua sosai itama Mama da sayyid akai musu ta dangana aka basu suka sha kafin aka samu Maman aka tafi da ita tareda Sayyid wanda shima Saida akai musu nasiha sosai akan zamansu anan bazai taba dawo da Ummitah ba wadda babu kaunar da zasu saka mata dashi bayan Su kaunaci ABDULAZIZ su tsaya akansa batareda sun bari duniyarsa da rayuwarsa ta mutu gabaki daya akan rashintaba. Wannan tinin da Mahaifinsa yayi masa ya sakasa jin duk wani asalin tsananin so da kaunar dayakewa Ummitah suna komawa akan Hammanta wanda zata iya bada rayuwarta akansa idan tana raye. Babu zaman gaisuwan da zaayi dan haka Alh saad na barin garin dasu aka watse cikeda radadi da ciwon rashin Ummitah tareda tausayin yanda rayuwa zataiwa ABDULAZIZ a yanxu da babu ta baida jininsa ko daya a duniya sai abinda Ummitah tabar masa. Tinda aka haifi babyn daga Mama har Sayyid haryanxu babu wanda yasan yanda take sbd kwata kwata sunma manta da ita matar mahaifin sayyid dince take kulawa da ita tinda suka isa . A hanyar komawan nasu Anty maryam ce take dauke da babyn wadda sai alokacin itama ta budeta ahankali ta zuba mata idanuwanta tana kalla. Sanyi jikinta yake dauka cikin tsananin tausayi da mutuwar jiki tana kallan kamannin Ummitah da ABDULAZIZ dake shimfide akan fuskan babyn wadda tin a yanzu da kammaninsu ta shigo duniyar wadda babu komai a cikinta sai son kai da son zuciya da gwagwarmaya tareda kaddarori masu kyau da marasa kyau. Ahankali ta sauke numfashi tana kai hannunta cikin sanyin jikinta daya tsananta ta rufe fuskan babyn sbd sanyin Ac dayake motar duk da an ragesa sosai sbd Babyn. Yamma sosai suka iso Abuja suka fara sauka gidan ABDULAZIZ din Alh saad yayiwa Mama da sayyid yar nasihar hakuri da dangana kafin suka wuce bayan Anty maryam ta nanatawa fiddausi kulawa da komai na babyn dasu maman da basa cikin walwala da nutsuwarsu. Suna ficewa Sayyid yashige yayi alwala ya fita sallan magrib bai dawo ba acan ya tsaya yana karatun Alqurani yana kuka kaman zaciyarsa zata fito kozai samu sassaucin abinda yakeji a kirjinsa. Yana ishai ya dawo gidan ya shige dakinsa bai sake fitowaba saida safe. Mama ma da daddare bayan Fiddausi ta gama bawa babyn madara ta sauya mata kaya da pamper sbd batai mata sabon wanka ba tinda bata iya wankan jariraiba, Dakin maman taxo tayi sallama ta bude tashigo rungume da babyn dake bacci cikin nutsuwar maraici da batasaniba. Dago idanuwanta da sukai laushi sosai mama tayi ta zubawa hannuwan Fiddausin datake tinkarota da babyn ta miqa mata. Hannuwanta rawa suka fara ta dagosu tana jin rawar zuciya ta karbeta tana dorawa akan kafafunta tareda bude fuskanta dake rufe, Tana saukar da idanuwanta akan fuskan babyn bata san lokacinda kuka me qarfin gaske ya kufce mataba tana qanqame babyn wanda take sak mahaifiyarta da tana jinjira. Fiddausi ma hawaye ne suka fara gangaro mata wainda taketa riqewa rashin Ummitah da tausayin megidan da baya nan dana sayyid sai kuma na babyn. Kuka sosai mama takeyi wanda ya saka Sayyid fitowa sbd yana jiyo kukan sbd kofar dakin a bude suka barta dan haka ahankali ya tako ya nufo dakin. A kofar dakin ya dakata idanuwansa na sauka akan fuskar 'yarsa wadda yake hango yanayin kamannin matarsa akan fuskanta. Ja idanuwansa sukai yanajin tsananin sonta dabaisan yaya zaiyi da zuciyarsa da rayuwarsa ma. Kallanta yakeyi ba tareda ya qarasa ba ya juya yana barin gurin sbd kukan maman dayake qaruwa yana kankaro masa ciwon dayake kokarin daurewa. Fiddausi ma juyawa tayi ta fice da dakin cikin tsananin tausayin mama dake jin inama fatima da Ummitah suna duniya su tayata kulawa da ABDULAZIZ da tasan zarewa zaiyi. A daren mama kwana tayi rungume da yar da har lokacin basama tinanin sunan da zaa saka mata huduba ma Baba alhassan ne yayi mata yace sai ABDULAZIZ ya dawo ya saka mata sunan daya dace. Washe gari da safe su anty maryam suka dawo gidan da mutane tareda maqota dake shigowa gaisuwa anata jajantawa tareda yiwa babyn data bari fatan rayuwa me albarka. #MAMUH #AZIZ AY LIMBA #FALAQ LIMBA #SAYYEED ZAFAFA BIYAR KALBIM 500 mamuhgee A DUNIYATA 500 Huguma AJIYA A DUHU 500 Billyn Abdul KIRJIN ME HANKALI 500 Miss xoxo Pay at 0022419171 AccessBank Maryam sani gummi Shedan biya 09033181070 Or mtn vtu at 09032345899*_Arewabooks@Mamuhgee_* 25 *ZUZEAM VENTURES* Best APHRODISIAC 08144015291 Aslm barkanmu da wannan lokaci Ina Mai farin cikin sanar daku cewa Zuzeam ventures takawo maku ingantattun magunguna masu inganci cikin Aminci Muna da kaya kamar haka Mallaka Maganin sanyi Maganin cire tumbiMaganin farin jini Maganin matsiMaganin mata Maganin sa ni’ima da dandano Dulka Amare Set na gyran jiki Set na amarya Tabaje tsumin Gomba Xuma kiba ta hips and Brest Magungunan gyran Brest Magungunan Karin hips Maganin sliming Muna da kaya masu inganci cikin sauki da rahusa Ina wadda keneman mallaka sahihiya quaranty wlh hajiya kixo ga zuzeam ventures xakiji ddin mallaka duk fadin ran ogah duk fadansa wlh sai yyi sanyi 08144015291 Idan maganin mata kikeso akwai Idan gyran jiki kikeso gyran fata gyran Brest magungunan sa kiba da hips DOMIN samunta Kai tsaye kira wannan no 08144015291 DOMIN mgn da ita whatapp 08144015291muna tura kayanmu ko ina cikin iKon allah 🥰👌🏻 Bononza Bononza Tsimin mangoro 1k🥭 Tsimin dabino 1k Gumba ukku balai 700 Gumba aya da nonon rakumi 700 Garin kafi ciccibi 500 Garin bata gaban kishiya 500 Matsin mallaka tada zaune tsaye 2500 Turaren mallaka ba aba mai kishiya 2500 Total kayan 9500 Za a bakisu akan 3800 Kuma mutun goman farko nadakyautar Abun 2k 🗣️🗣️🗣️🗣️🗣️🗣️ ASSALAMU ALAIKUM ALHAMDULILLAH YAN UWA NEW PROMO YA KAMMALA💃🏽💃🏽💃🏽😁😁😁 da 5k dinki ki kwashi kayan 12k hajiyata 💃🏽💃🏽💃🏽😃🙃Kazar gadali ta mallara Rabi 3500 Tsimin gam gam 1500 Ruwan kara zunzurutun dadı😋800 Garin 7in1 1k Gumba 3 balai 500 Gumba kwakwa da dabino 500 Infection ruwan tsarki 1k Garin zunzurutun dadi 1200 Matsin ba a fira d wando 500 Matsin infection mai matse mace gam 500 12k All at 5k kedai dannan link dinnan don samun naki ki maza kiyi bucking koda kudinki saida Rabonki *********A ranar da Ummitah tabar duniya ana ficewa da gawarta asibitin a lokacin aka shiga aikin JANNAH ZAADEN wadda aka shiga da ita iyayenta na kofar dakin tiyatar suna hana kunnuwansu daukan sautin ihu da karar kukan yan uwan Ummitah dake cikin tsananin quncin rashinta Suna maida dukkanin hankalinsu da nutsuwarsu tareda fatarsu akan samun nasarar da zata bawa Jannah sabuwar rayuwar da suketa gwagwarmaya akai. Dukkaninsu basu taba shiga tsananin lokaci irin wannan ba a rayuwarsu na jiran dayake saka zuciyoyinsu muguwar bugawan da babu wanda jininsa bai iya hawaba a lokacin. Securities ne a zagaye da gurin amma sam basu bari hakan ya zama obvious ba amma kwata kwata ko motsin komai bakaji a gurin. DZAD,DADDY MAHMOUD,MIMI,MOMMY(matar daddy Mahmoud),LUBNAH(yar riqon mommy) sai Maheer wanda ya kasa zama time kawai yake calculating yana jin maqoshi nsa na bushewa,sai Saleem wanda shima yake jin kaman ya shiga dakin tiyatar ya ganowa idonsa ko zai samu sassaucin abinda yake ji. Dukkanin familyn suna zaune ne babu wanda zuciyarsa ba bugawa takeyi ba da sauri da kuma faduwar gaba. Su mimi basusan meya faruba kawai abinda suka sani shine an samu donor wanda yayi a lokacinda suka cirewa Jannah rai dan haka suke fatar a dace sbd daga baa dace dinba shikenan wannan karan jannah zata zaka tarihi a rayuwarsu sbd ta lokaci da ake tinanin nata yayi yayi din. Wutar kofar dakin da aka kashe ce ta saka dukkaninsu miqewa tsaye idanuwan Mimin na gangarowa da wasu hawaye masu dumi. Dzad kuwa jajayen idanuwansa ya dago ya kalli kofar kirjinsa na wani irin nauyin daya sakasa dafe kirjinsa har Maheer na saurin riqesa. Daddy mahmoud ne yayi karfin halin bude bakinsa yana kallan Ammar daya fara fitowa idanuwansa jajir wasu hawayen farin ciki na gangaro masa, Kallo daya yayiwa Mimi hawayensa suka qara gudu baice komaiba ya ware Hannuwansa ta fada jikinsa ya rungumeta da Qarfi. Dr Abraham ne da Anny suka fito a tare tana zare maska dinta tana kallan mijinta itama cikin farin cikinta dayake bayyane. Dr Abraham cikin sauke numfashin shekarun fama ya zare mask dinsa Yana kallan Dzad yace "It was a success atlast sir" Kuka Mimi ta fasa me sauti tan qanqame Ammar wanda shima yake hawaye yana dariyan farin ciki. Maheer Anny ya warewa hannuwansu ya rungume yana cewa "ALHAMDULILLAH" Dad Zuciyarta kusan kasa daukan farin tai ya zame ya zaune kirjinsa na masa nauyi. Daddy Mahmoud dr Abraham ya miqawa hannu fuskansa cikeda farin ciki yana masa godia tareda kyautar data saka dr Abraham din sake miqa masa hannu cikin farin ciki. Saleem ma Dad ya rungume yana cewa "ALHAMDULILLAH Dad" Dad kasa magana yayi kirjinsa ya riqe dole akai gaggawar nufar dakin hutawa dashi dr Finn zai dubasa. Fitowa akai da Jannah a gado ana turawa cikin nutsuwa ahankali dukkaninsu suka miqe tsaye yana zuba idanuwansu akanta zuciyoyinsu fal farin ciki da fargaba tinda ba ganinta sukai ta miqe ba. Kyakkyawan fuskanta data rame sai dogon hancinta dayake a tsaye dukkaninsu suke kalla suna godewa Allah da ganin wannan rana. Bayanta suka dunguma zuwa private dakin da aka nufa aka kwantar da ita dr Abraham da Ammar suka qarasa dukkanin abinda zasuyi da rubuce rubuce da komai Dr Abraham ya fice shima Ammar wucewa yayi ya nufi gida sbd kwanansa biyu a asibitin bai fitaba. Gida ya nufa dan wanka da cin abinci da samun nutsuwar dayake jin a shekaru bai samuba. Suma Mimi godia suka ringa yiwa Allah Mimi nayiwa Wanda zuciyarsa take jikin Jannah din tareda danginsa kaf da fatar zata samu damar saninsu tayi alkhairin da bata taba yiba arayuwarta dan kuwa zata tattara duka gwalagwalanta ta basu koda kuwa sunada arzikin to su qara sbd batada abinda zata biyasu dashi duniya da lahira. ******ABDULAZIZ duk yanda yaso yayi magana dasu Ummitah abin ya gagara sbd wayar Ummitah bata shiga,ta mama tana ringin baa dagawa ta sayyid ma bata shiga, Alh saad yace masa suna nan lafiya hakama anty maryam idan ya kirata akan yanason magana dasu magana daya take fada masa data Alh saad din. Kwata kwata yau kwanaki biyar kenan yana wani irin ciwon dabai san meyake damunsa ba haka kawai ciwon kirji da zuciya yake har jiri sai yana dibansa wanda daga karshe dole yaga dr karshe admitting nasa akai likita yace stress ne da damuwa kawai daya sakawa kansa. Sosai ya kwana asibitin wanda ya saka likita hanasa ko taba wayoyinsa aka kashesu. Amma hakan kusan hana zuciyarsa samun nutsuwa yayi wanda yake jin yana rasa nutsuwarsa da hankalinsa kwata kwata dole doctors suka basa wayarsa dan yayi magana da familynsa dan samun nutsuwa. Wayarce gabaki daya ta kasa samuwa yanda yakeso sbd a cikin mutum uku da suke familynsa kwata kwata ya kasa jin ko daya dan haka kai tsaye ya nemo numbern drivernsa Latif wanda yake bayerabe ya saka kira. Kiran na shigowa wayar latif gabansa yayi mummunan faduwa sbd bai kira yayi masa gaisuwaba sbd tsoro da tausayin halinda yake ciki jin rasuwar Sanyin idaniyarsa dama su gaba daya tinda suna sonsa dole sike kaunar Ummitan sosai. Tana gap da katsewa ya daga kiran cikin tsananin sanyin muryan data saka ABDULAZIZ din sauke ajiyar zuciya. Gaidasa Latif ya fara cikeda girmamawa yana rasa ta inda zai fara masa gaisuwa. Kafin ya amsa gaisuwarsa kai tsaye da muryansa datai kauri kirjinsa a toshe da bacin ran yanda kowa a gida wayarsa ta koma kaman batada amfani a taqaice yacewa latif "Inason magana da mama,Sayyid or Ummitah ka kaiwa daya daga cikinsu wayar........ Tsabar rudewa Latif da yarensa yace "Sir you say??? Cikin hade fushinsa yace "Do i have to repeat wat i said?? Da sauri latif na qarasa ridewa ya nufi cikin gidan yana hada gumi yace "Yes,no no sir" Duk ya rikice ya rasa me zaice jin sunan Ummitah dan haka ya qara sauri zuwa cikin gidan yana godewa Allah dabaiyi saurin yi masa gaisuwaba yafara ji daga bakinsa.. Yana knocking kofa fiddausi dake palo tana hadawa Baby madara tanata kuka me qarfi ga mama tana sallah Sayyid ma yana masallaci ta taso ta bude kofar wanda ya bawa ABDULAZIZ saukan kukan babyn kai tsaye cikin kunnuwansa daya sakasa tashi ahankali daga zaunen dayake zuwa tsaye yana dago wayar daga kunnuwansa ya kalla ya sake mayarwa yayi shiru kukan babyn me qara yana shiga kunnuwansa sbd tana hannun Fiddausi data taso ta bude kofar tana kallan Latif daya miqa mata wayar da sauri muryansa har tana rawa yace "Sir na son magana da Mama or oga Sayyid and...... Shiru yayi yana kallan babyn da sai alokacin ya tina da Sir din zaiji kukanta. Fiddausi na jin abinda ya fada tayi baya tana qin amsar wayar ta juya da sauri dan kiran mama. Hanata tafiya latif yayi yana gwale mata idon ta karba kada tai masa haka dan yasan yana saka wayar a kunnensa maigidan zai iya jeho masa kowace irin tambaya. Fitowan mama tana idar da sallah batareda ta tsaya addua ba sbd kukan babyn ya saka latif saurin jeho qafa palon da sauri ya miqawa mama wayar tana amsa ya juya da sauri. Fiddausi ma barin palon tayi jikinta a sanyaye. Mama saida wayar ta shiga hannunta ta gane waye akai take qafafunta sukai sanyi daidai lokacin sayyid ya shigo palon hakama Babyn a lokacin ta sake fasa wani kuka me qarfi na jirirai sabuwar haihuwa ba kakkautawa wanda hake shiga kunnuwan ABDULAZIZ direct yana wucewa zuwa zuciyarsa da bugunta ya sauya ya kasa cewa komai sbd yanda yakejin kukan babyn har cikin tsakiyar zuciyarsa ya tabbatar masa da kukan babyn Ummitah ne. Shiru dukkaninsu sukai har Sayyid wanda yaga sunan SIR LIMBA akan wayar hannun mama ya san shine take jikinsa yayi mugun mutuwa radadin zuciyarsa na dawowa sabo. Shirun lokaci mai dan tsayi sukai kafin ya iya bude bakinsa da yayi masa nauyi jin bazasu fada masa komaiba bayan sunsan yaji kukan babyn da sauti me tsananin nutsuwa da sanyi yace "Ummitah ta haihu ne??? Shiru sukai hawaye na gangarowa mama tana qanqame babyn jikinta. Shiru ya dan yi yana jiran amsarta kafin ya sake cewa "Ummitah kece? Kin sauka dinne? Kukane yake kokarin kwacewa mama ta miqawa Sayyid babyn wanda yaune ranar farko data shiga hannuwansa. A tsananin taushin sautin dayake sake qara nauyin zuciyarsa yace "Ummitah?? Kuka me qarfin gaske mama ta fashe dashi tana kasa riqewa sbd yanda yake ambatar Ummitan da bazata amsaba har abada sai lahira kila.. "Mama" ya furta cikin tsananin mamaki da sanyi yana cewa "Mama kuna lafiya? Lafiya kuwa? Meyake faruwa ne wayoyinku basa tafiya? Ummitah ta haihu dinne mama??? Maganganunsa kashe mama sukeyi kukanta na tsananta ta kasa cewa komai Jin ya kasa jeho tarin tambayoyin dake kasheta cikin kuka mai ratsa zuciya da kashe jiki tace "ABDULAZIZ kana buqatan dawowa, Muna tsananin buqatanka a gida..... Rintse idanuwansa yayi abinda yake ji yana fara fin karfinsa daga lokacinda take kukan daurewa kawai yakeyi dan haka cikin tsananin karfin hali da dauriya ya bude baki yace "Mama zan aje duk abinda nake na dawo, Ina Ummitah?zanyi magana da ita" Sayyid na jin hakan ya juya yabar gurin rungume da babyn wadda tayi shiru a jikinsa tana sauke numfashin bacci da zata koma. Mama shiru tayi ta kasa basa amsa kukanta na komawa sbd tsoron abinda batasan me zata fada masa ba. Ajiyar zuciya me sanyi ya sauke ahankali cikin sake nutsar da kansa yace "Mama nace insha Allah duk abinda nake nabarsa zan dawo, A kiramun Ummitah, Kuma baki ban amsan haihuwan ba, Ummitan na lafiya?yaya babyn itama lafiyanta kalau? Ko akwai matsala ne mama?? A cikin wani azababben ciwon daya taso ya danne zuciyarta da sabon kukan data kasa riqewa tace "ABDULAZIZ MUNYI MUMMUNAN RASHIN DA HAR ABADA BAZAMU WARKEBA DAGA GARESA" #MAMUH #AZIZ AY LIMBA #JANNAH ZAADEN #ZAADENS #SAYYEED ZAFAFA BIYAR KALBIM 500 mamuhgee A DUNIYATA 500 Huguma AJIYA A DUHU 500 Billyn Abdul KIRJIN ME HANKALI 500 Miss xoxo Pay at 0022419171 AccessBank Maryam sani gummi Shedan biya 09033181070 Or mtn vtu at 09032345899*_Arewabooks@Mamuhgee_* 26 *ZUZEAM VENTURES* Best APHRODISIAC 08144015291 Aslm barkanmu da wannan lokaci Ina Mai farin cikin sanar daku cewa Zuzeam ventures takawo maku ingantattun magunguna masu inganci cikin Aminci Muna da kaya kamar haka Mallaka Maganin sanyi Maganin cire tumbiMaganin farin jini Maganin matsiMaganin mata Maganin sa ni’ima da dandano Dulka Amare Set na gyran jiki Set na amarya Tabaje tsumin Gomba Xuma kiba ta hips and Brest Magungunan gyran Brest Magungunan Karin hips Maganin sliming Muna da kaya masu inganci cikin sauki da rahusa Ina wadda keneman mallaka sahihiya quaranty wlh hajiya kixo ga zuzeam ventures xakiji ddin mallaka duk fadin ran ogah duk fadansa wlh sai yyi sanyi 08144015291 Idan maganin mata kikeso akwai Idan gyran jiki kikeso gyran fata gyran Brest magungunan sa kiba da hips DOMIN samunta Kai tsaye kira wannan no 08144015291 DOMIN mgn da ita whatapp 08144015291muna tura kayanmu ko ina cikin iKon allah 🥰👌🏻 Bononza Bononza Tsimin mangoro 1k🥭 Tsimin dabino 1k Gumba ukku balai 700 Gumba aya da nonon rakumi 700 Garin kafi ciccibi 500 Garin bata gaban kishiya 500 Matsin mallaka tada zaune tsaye 2500 Turaren mallaka ba aba mai kishiya 2500 Total kayan 9500 Za a bakisu akan 3800 Kuma mutun goman farko nadakyautar Abun 2k 🗣️🗣️🗣️🗣️🗣️🗣️ ASSALAMU ALAIKUM ALHAMDULILLAH YAN UWA NEW PROMO YA KAMMALA💃🏽💃🏽💃🏽😁😁😁 da 5k dinki ki kwashi kayan 12k hajiyata 💃🏽💃🏽💃🏽😃🙃Kazar gadali ta mallara Rabi 3500 Tsimin gam gam 1500 Ruwan kara zunzurutun dadı😋800 Garin 7in1 1k Gumba 3 balai 500 Gumba kwakwa da dabino 500 Infection ruwan tsarki 1k Garin zunzurutun dadi 1200 Matsin ba a fira d wando 500 Matsin infection mai matse mace gam 500 12k All at 5k kedai dannan link dinnan don samun naki ki maza kiyi bucking koda kudinki saida Rabonki ************* Shiru yayi yana gama sauroron bayaninta da bai gane inda ya nufa kafin ya sauke ajiyar zuciya ahankali ya bude baki da nutsuwa sautinsa na sanyaya yace "Mama meya faru? Me yake faruwa? Kukan dayafi na baya ratsa zuciya takeyi sosai tana kasa bude idanuwanta kaman yana gabanta tana breaking tace "Mun rasata gurin haihuwa...... Wani irin Numfashin daya saka maman kasa qarasawa ya sauke da wani irin sauti me tsananin nutsuwar son fahimtar abinda ya kasa fahimta yace "Ita Ummitan??? Kasa amsawa tayi sbd kukan dayaci karfinta mara sauti. Dif taji yaji kashe wayar batareda yace komaiba. Wani mummunan jiri ne ya dibesa kafafunsa suka sare da karfi gwiwowinsa suka daki qasa da karfi wayar hannunsa na faduwa qasa. Rawa hannuwansa suka dauka ya miqasu da sauri yana lalubar wayar hannunsa data fadi sbd ganinsa dayake kokarin daukewa da jinsa dab dif yake jin. Yanda hannuwansa ke rawa sosai yasaka ya kasa samun inda wayar take duk da tana gabansa sam baya gani. Kokarin kasa bugawa zuciyarsa keyi amma ya kasa barin hakan, Hannuwansa ya saka ya murza idanuwansa da karfin daya kusan raunana kansa kafin ganinsa kadan ya dawo ya duba wayar da sauri ya dauka hannuwansa na tsananta rawar datake kokarin hana wayar tsayawa hannunsa. Daqyar ya iya gano sunan Alh saad sbd rashin ganin da yake sake rufe idanuwansa kwata kwata. Ringing din da wayar keyi duk daya tafiya yake da numfashinsa dayake fara sarkewa yana suffocating. Alh saad cikin nutsuwa ya dauki wayar tareda sallama cikin mutuwar jiki sbd duk lokacinda Ko sunan ABDULAZIZ din yagani jikinsa ke mutuwa. "Ummitah ta haihu?? Meya sameta? Tana ina? Inason magana da ita,No i want to See her on a Videocall, Meyake faruwa, Why are you quite? Meyasa mama ke kuka? Ina Ummitah. Say something.......... Alh Saad bai zubarda hawaye a rasuwar Ummitah ba amma take yaji idanuwansa na kokarin cikowa da hawayen dake girgiza jarumtarsa da manyancinsa sbd yanda Yana jiyo wani irin mummunan breaking da ABDULAZIZ ke kokarin a muryansa, Gabaki daya tamboyinsa baya hayyacinsa yake jehosu babu abinda yakeson ji bayan amsa daya. Acan bangaren cikin sautin daya tabbatarwa da Alh saad jikin ABDULAZIZ din yai tsananin sanyi da wata qasqantacciyar murya yace "Ta haihu? Is she okay? I really want to talk to her, Am coming back tomorrow amma i cant without hearing from her, Please, Please......a cikin wani irin mummunan sauti me tsananin sanyi da rashin kuzari ko kadan ya ringa maimaita pls dinsa data saka Alh saad karasa karyewa ya sunkuyar da kansa yana shanye hawayensa ya bude baki shima a sanyaye cikin tsananin rashin kuzari yace "ABDULAZIZ karka manta Duk mai zai dandana mutuwa, Ka rasa iyayenka ka samu dangana a yanzu ma zaka dangana ne sbd Allah ya riga ya karbeta sbd lokacinta ne yayi, Abinda ta haifa tananan Lafiya kalau ita kam sedai Mu bita da Add..... Dif yaji wayar batareda ya qarasa maganar dayake ba, Daga wayar yayi ya kalla yaga tabbas ta yanke, Saka kiransa yayi da sauri yana miqewa daga zaunen dayake. Ringing wayar takeyi harta yanke baa dagaba Sake saka kiran yayi yana fatan ya dauka sedai harta kuma yankewa baa dagaba. Cigaba yayi da kiran kaman mahaukaci shima yana fatar a daga amma baa daga dinba karshe ma shiru ta dena shiga kwata kwata. Damuwa yaji duk ta cikasa sbd baisan irin damuwar da ABDULAZIZ din zai shigaba gashi bai tsaya sauraransaba bare ya kwantar masa da hankali duk da yasan babu abinda zai kwantar masa hankali a yanzu idan ba addua zasu duqufa yi masa ba. Gaba daya zuciyarsa kasa nutsuwa tayi yaji hankalinsa yana kasa kwanciya dan haka ya dauki wayarsa ya kira Sayyid Wanda aka siyawa sabuwar babbar waya dal yana dauka Yace "Sayyid Kunyi magana ne da ABDULAZIZ? Numfashi Sayyid ya sauke ahankali kafin yace "Yayi magana da mama dazu sedai basu gamaba ya kashe tace" Numfashi Alh saad ya dauke yana sake shiga damuwa yace "Inata kiransa baa dauka, Waye ya sanar dashi?? Cikowa idanuwan Sayyid sukai da hawaye masu zafi yana kallan Babyn datake rungume jikinsa tayi bacci a sanyaye yace "Babyn Ummitansa ce ta sanar dashi da kanta ta iso duniya...... qarasa maganar yayi hawayensa na sauka akan gefen fuskanta har saida ta dan motsa kadan. Shiru Alh Saad yayi yana sake shiga damuwa da rashin nutsuwar zuciya yace "Kukanta ya sanar dashi an haihu kenan?? Kasa magana Sayyid yayi sai daga baya yace "Eh" "Sayyid kuyita kiransa a samu wani yayi magana dashi pls kaji" "Ok insha Allah" Sayyid ya fada a sanyaye. Kashe wayar Alh saad yayi take Sayyid din ya saka kiransa sedai ma ko tafiya batayi yana saka kiran kiran yake yankewa da kansa. Ringa saka kiran yayi ba kakkautawa amma babu alamar ma kiran zai tafi. Fitowa yayi ya bawa Fiddausi babyn ta goyata shi kuma ya fita yanata sake kiran Hamman zuciyarsa na tsananin jin son magana dashi sbd tinda Akai rasuwar haryanzu bakinsa da nasa bai haduba bayan yana buqatan jin muryan Hamman ko zai samu Sassaucin rashin Jinin Hamman da yayi. Mama ya dawo ya sanarwa Baa samun ABDULAZIZ din dan haka itama ta dauko wayarta kowannensu yanata kira amma ba saa. Har dare suna kiransa akai akai amma sam babu sauyi. Da daddare mama da kanta ta shirya babyn a cikin kayan sanyi masu tsada da kyau ta kwantar da ita gefenta tareda Zuba mata idanuwanta tana tina ranar farkon haduwarta da Fatima Asalin mahaifiyarsu ABDULAZIZ din wanda tin daga lokacin kauna me karfi da tsafta a tsakaninsu. Fatima ta tafi tabarta, Inna ma ta tafi tabarta, Ummitah ta tafi tabarsu itama tabar musu 'ya kaman yanda Fatima ta tafi tabar musu Ummitan tana qarama, A yanzu batasan yaya zatai da ABDULAZIZ datasan duniyarsa ta rushe gabaki dayanta, Yaushe zai samu farin Zamowa ahali daya daya rage a zuriar fatima, A yanzuma zai sadaukar rayuwarsa ne gurin kulawa da tattali tareda ingata rayuwar 'yar da Ummitah tabar masa, Yaushe zai samu rayuwar farin ciki da walwala kaman kowa?? A yanzu basusan halinda yake cikiba a can qasar dayake daya samu wannan mummunan labarin. Hawaye ne sike gangaro mata ahankali ta gefen ido suna sauka akan pillon da kanta yake kai batareda ta dauke kallanta daga kan babyn wanda itama Sunan Fatimar ne sunanta sbd Shine Sunan da ABDULAZIZ yakeso fiyeda kowane suna kuma shine sunan dayace zaa sakawa Babyn daman idan an haifeta sbd Ummansa Fatima ce hakama Ummitansa Fatima ce dan haka a yanzu ma ga wata fatimar ya samu wadda tasan zai iya bada rayuwarsa akanta itama. Sayyid kwana yayi yana kiran Hamman sbd gaba daya yaji shima bayajin nutsuwa tinda baya tareda su yasan yana can cikin mawuyacin mummunan halin dayafi duk wanda suka shiga baida wanda zai rungumesa ya rarrashesa bare quncin rasuwar Ummitah yana ninkuwa ne sbd ko gawarta bai samu gani ba bare janazah dinta wanda har abada bazai dena jin wannan radadinba a zuciyarsaba kuwa. Shi kansa Alh Saad akai akai ya ringa sake kiran Amma ba bayanin komai. Washe gari Sayyid duka yan gidan saida ya karbi wayarsu ya ringa kiran Hamman Amma sam duk abu daya ne batama alamar shiga take yankewa. Haka suka wuni cikin damuwa da sanyin jiki suna nemansa babu haske ko kadan. Washe gari ma hakan ce ta faru har aka sake kwana suna kan abu daya. Alh Saad suka kira suka sanar masa ya kwantar musu hankali da cewan ABDULAZIZ din a ranar da sukai magana ya sanar dashi zai dawo a washe gari amma tinda an kwana biyu a sake basa kwana biyu a gani tukuna kila ya daga tafiyar ne sbd shock na rasuwar. Hakura sukai suka zuba idanuwan dawowan nasa duk da hakan bawai sun dena kiran bane musamman Sayyid dayake jin yana neman sabuwar zarewa Mama kuma kulawa da babyn yana dan hanata damun lokacin kanta ma sbd ga manyanci ne ga kula da jaririyar 'ya duk da ga Fiddausi tana kama mata sosai danma wani abin bata iyawa sedai Fiddausin tai mata. Baba alhassan ne ranar da akai bakwai ya iso da manyan ragunansa guda biyu da na yankawa jaririyar suna. Dayake ba wai hidimar farin ciki akeba yasaka addua kawai akai aka yanka mata Sunan FATIMAH kaman yanda sukasan ABDULAZIZ yakeda buri. Koda Baba alhassan ya iso shima Alh Saad ya riga ya siya ragunan suna dan haka aka hada duka aka yanka akai sadaka sosai tareda yiwa mahifiyar babyn Addua dashi kansa ABDULAZIZ da basusan halinda yake ciki. Baba alhassan bai komaba sbd ganin rayuwar qunci da 'dacin dasu Sayyid sukeyi gashi shima ya shiga tsoro da damuwar rashin ABDULAZIZ din dan haka ya fasa tafiya sai ansan halinda yake ciki. *****Lamarin da tin suna lissafi har suka dena suga shiga mummunan damuwar datake take rashin da sukai sbd kwata kwata ba ABDULAZIZ ba labarinsa sun duqufa rokon Allah da sadaka, Mama ta rame sosai ciwo yana neman rufe rayuwarta sbd damuwa da tinani, Sayyid ma ya koma gabaki daya ko magana bayayi sosai daga daki sai masallaci dayake kusan wuni acan yana karatun Alqurani da adduar bayyanar ABDULAZIZ tareda fatar yana cikin koshin lafiya. Baba alhassan ma gida ya koma aka ringa yiwa ABDULAZIZ din adduar dangana akan rashin da yayi da fatar yana cikin koshin lafiya. Alh Saad duk inda zai saka a dubo masa ABDULAZIZ a bincika masa shi a italy abin ya gagara sbd dukkanin wasu hanyar communication da zaa iya jinsa ko labarinsa ta toshe musu sbd Alh saad duk wanda ya sani a qasar italy dazai duba masa shi basa qasar daman duka duka mutum biyu ne ya sani acan baida mutane acan ba kamar uk ko Greece ba ko wasu daidaikun qasar. Dan haka shima hankalinsa ya tashi sosai gashi ana maganar wata uku ba labarin komai, Su mama sun koma abin tausayi sosai sbd ciwon tsaye takeyi gadan gadan, Sunso tattarawa su koma gida shikuma Sayyid yana tinanin kota halin yaya zai neme abinda zai kaisa qasar da ABDULAZIZ din yake ya nemesa sbd zuciyarsa radadi takeyi masa sosai yanaji a jikinsa ABDULAZIZ na cikin matsanancin halinda yake buqatansu. Mama kuwa gaba daya a yanzu tafara gazawa dan haka Alh Saad ya hanasu komawa gida yace su zauna anan Shi zai tafi qasar ya dubo ABDULAZIZ da kansa. #MAMUH #AZIZ LIMBA #FALAQ LIMBA #SAYYEED LIMBA #ZAADENS ZAFAFA BIYAR KALBIM 500 mamuhgee A DUNIYATA 500 Huguma AJIYA A DUHU 500 Billyn Abdul KIRJIN ME HANKALI 500 Miss xoxo Pay at 0022419171 AccessBank Maryam sani gummi Shedan biya 09033181070 Or mtn vtu at 09032345899*_Arewabooks@Mamuhgee_* 27 *ZUZEAM VENTURES* Best APHRODISIAC 08144015291 Aslm barkanmu da wannan lokaci Ina Mai farin cikin sanar daku cewa Zuzeam ventures takawo maku ingantattun magunguna masu inganci cikin Aminci Muna da kaya kamar haka Mallaka Maganin sanyi Maganin cire tumbiMaganin farin jini Maganin matsiMaganin mata Maganin sa ni’ima da dandano Dulka Amare Set na gyran jiki Set na amarya Tabaje tsumin Gomba Xuma kiba ta hips and Brest Magungunan gyran Brest Magungunan Karin hips Maganin sliming Muna da kaya masu inganci cikin sauki da rahusa Ina wadda keneman mallaka sahihiya quaranty wlh hajiya kixo ga zuzeam ventures xakiji ddin mallaka duk fadin ran ogah duk fadansa wlh sai yyi sanyi 08144015291 Idan maganin mata kikeso akwai Idan gyran jiki kikeso gyran fata gyran Brest magungunan sa kiba da hips DOMIN samunta Kai tsaye kira wannan no 08144015291 DOMIN mgn da ita whatapp 08144015291muna tura kayanmu ko ina cikin iKon allah 🥰👌🏻 Bononza Bononza Tsimin mangoro 1k🥭 Tsimin dabino 1k Gumba ukku balai 700 Gumba aya da nonon rakumi 700 Garin kafi ciccibi 500 Garin bata gaban kishiya 500 Matsin mallaka tada zaune tsaye 2500 Turaren mallaka ba aba mai kishiya 2500 Total kayan 9500 Za a bakisu akan 3800 Kuma mutun goman farko nadakyautar Abun 2k 🗣️🗣️🗣️🗣️🗣️🗣️ ASSALAMU ALAIKUM ALHAMDULILLAH YAN UWA NEW PROMO YA KAMMALA💃🏽💃🏽💃🏽😁😁😁 da 5k dinki ki kwashi kayan 12k hajiyata 💃🏽💃🏽💃🏽😃🙃Kazar gadali ta mallara Rabi 3500 Tsimin gam gam 1500 Ruwan kara zunzurutun dadı😋800 Garin 7in1 1k Gumba 3 balai 500 Gumba kwakwa da dabino 500 Infection ruwan tsarki 1k Garin zunzurutun dadi 1200 Matsin ba a fira d wando 500 Matsin infection mai matse mace gam 500 12k All at 5k kedai dannan link dinnan don samun naki ki maza kiyi bucking koda kudinki saida Rabonki. ********* Tafiyar da Alh Saad yace Zaiyi ya saka Maman da Sayyid samun dan sassaucin Halinda suke ciki. Baba alhassan na jin hakan shima Ya tattara ya koma gida dayake ya sake zuwa sbd Yiwa Sayyid abinda yake tsananin so yana komawa ya saka gonarsa siyarwa da rabin hatsin daya noma a shekarar yayi kwana biyu yana hada kudin ya dawo da kudi me dan yawa kusan miliyan uku ya kawowa Sayyid suka kaiwa Alh Saad akan a tafi da Sayyid din dubo ABDULAZIZ din. Itama mama jin hakan ta sake samun sanyi a ranta suka ringa rokon Alh ya tafi da Sayyid din. Sbd kwanciyar hankalinsu ya amince tafiyar dashi batareda ya karbi kudinsu ba sbd yasa aka fara yiwa Sayyid din komai na tafiya wand hakan ya saka tafiyar ta sake samun tsaiko. Baba alhassan duqufa yayi da addua da fatar komai ya tafi lfy sbd a zuciyarsa tsoro yaji yana shigarsa. Mama ma adduar ta sake duqufa yi gashi a kwanakin kullum mafarkin ummitah takeyi wanda take ganin ABDULAZIZ ne a cikin wata masifar kila. Sbd Lokacinda Ummitah zata rasu mafarkin ABDULAZIZ din ta ringa yi a mummunan yanayi sai gashi ashe rasa Ummitah zasuyi. Sayyid haka ya ringa jin kaman zai zare sbd jiran shirin tafiya ya kammala visa ta fito, Karatunsa da Alh Saad ya takura masa yaci gaba da zuwa Sosai ya maida hankali kaman zai kwana ya tashi a ace ya kammala sbd tsananin burin da ABDULAZIZ ya dora akan karatunsa tin farko yasa duk masifar da zuciyarsa take ciki ya tsaya ba gardama yana bude kansa sosai akansa. Baba alhassan kuwa komawa yayi duk bayan lokaci yana hanyar zuwa abujan dubosu. Baby Fatima kuwa anata renonta cikin koshin lafiyarta tana girmanta duk da bata samu nono ba jikinta nata yin kyau tana yar kibarta, Anty maryam sbd basada nisa a anguwa daya suke bata tsallake ranar zuwa duba Baby fatiman da Mama wani lokacin kuma zuwa take ta dauketa acan zata wuni sai dare take kawota a mota dan basa bin hanya da ita duk da da nisan da sai anshiga motar. Wata daya da sati biyu suka dauka kafin tafiyar ta kammalu suka tsayar da rabar tafiya. Mama Kallan Sayyid tayi ranar da zasu tafin tana rungume da Baby Fatima ta zuba masa ido tana kasa iya cewa komai sbd batama san me zata fadan ba. Baby fatima ya kalla kafin ya kalli maman yana bude baki Ahankali yace "Mama nai miki Alqawarin zan dawo miki da ABDULAZIZ LIMBA a gabanki ko a yaya yake insha Allah sannan zan kula dashi fiyeda nawa kan" Numfashinta ta hidiye cikin sanyi da samun dan sanyi a ranta tace "Allah ya tsareku gaba daya ya dawo daku lfy yasa shima yana lafiyar" Alh Saad ta kalla cikin mutuntawa da kulawa tace ta gode. Baba alhassan ma addua yayi musu yana yiwa Alh Saad godia. Mota suka shiga drivern gidan Alh Saad dinne zai kaisu Airport su mama na kallo motarsu ta fice daga gidan. Ajiyar zuciya Baba Alhassan ya sauke ita kuma Mama kasa sauke ajiyar zuciyar tayi ta juya ciki tana sake rufe Fatima dake bacci a jikinta tana dan motsawa ahankali. Tinda suka isa airport Alh Saad ya kalli Sayyid wanda kai tsaye kallo daya zakai masa kasan ya sauya daga asalin Sayyid dinsa na baya idan ka sansa. Har a cikin jirgi bayan sun zauna babu walwala a tattareda Sayyid din dan haka bai takurasa ba ya kyalesa dan yasan zuciyarce ba dadi ko kadan. ****** Lafiyayyan toilet ne dayake da girma sosai komai a tsare, Qamshi ne me sanyin dadi da nutsuwa yake tashi a cikinsa hakama da dan hayaqin zafin ruwan da ake wanka dasu dayake dan gauraya toilet din yana saka koina a toilet din daukan dumi ahankali. Wanka takeyi a natse qamshin shower gel dinta me kyau da tsada yana sake tashi harta gama wankan ta kashe shower din tareda miqa hann ta janyo towel ta dauro a jikinta ta fito cikin Lafiyayyar jacuzzi din ta nufo gaban mirror daya kusan cike rabin bangon toilet din ta tsaya cak ta zubawa kanta idanuwanta da suka fara sauyawa ahankali. Hannunta na dama ta dago ahankali ta dora akan kirjinta seti da zuciyarta dake bugawa ahankali cikin cikakkiyar lafiya.. Tabon dinkin gurin ta shafa ahankali tareda lumshe fararen kyawawan idanuwanta tana sauke numfashi ahankali me dumi... Tin daga lokacinda ta wayi gari ta samu kanta a sabuwar rayuwa daukeda sabuwar zuciyar datake bugawa a kirjinta tasan duniyarta ta sauya ta dawo sabuwa a daidai lokacinda ta cire rai da rayuwa gabaki dayanta, Allah ya bata damar cigaba da rayuwa a lokacinda take saka ran ta farko ta samu kanta a duniyar barzahu, Duk wanda zuciyarsa take bugawa a kirjinta tana masa fatar samun rahamar ubangiji dashi da danginsa a duk inda suke, Harta bar duniya bazata dena yi masa addua ba sbd sadaukarwansa gareta. Ajiyar zuciya ta sauke ahankali tana lumshe idanuwanta tana sake jin bugun zuciyar wadda take tata ayanzu yana ratsata cikeda shauqi da samun nutsuwa da yanayin da bata saniba a baya na bugawar Lafiyayyar zuciya a kirjinta. Ayau kusan wata hudu da kwanaki kenan da aikinta amma haryanzu ta kasa sabawa da sabuwar rayuwar data samun koyaushe jinta takeyi kamar sabuwar mutum sedai kauna da tsananin son datakewa yan uwanta familynta babu abinda ya sauya saima qaruwa da yayi sbd jajirwansu gareta. Kaman yanda samun lafiyarta ya sauya rayuwarsu gaba daya a qanqanin lokaci sbd sabon farin ciki da jin dadine tareda sabuwar rayuwa ta dawo musu sabuwa dan haka komai nasu ya dawo tamkar baya kusan ma fiye dan farin ciki da kwanciyar hankalin dasuke dashi yanzu na tafiyar da komai yafi na bayan. Ta jima a tsaye kafin ta juya ta fito toilet din. Qamshin dayake tashi a bedroom din nata ne ya shiga hancinta ta dan Lumshe ido tana jinsa yana ratsata sbd komai a yanzu jinsa take kamar sabo gareta. Gaban mirror ta nufa bayan ta zaro wani towel din tana goge jikinta a hankali kamar batason taba soft fatarta sosai. Da kanta ayau ta shirya kanta sabanin tinda suka gama jinya a asibiti suka dawo gida Mimi ke tayata shiri sbd batason tayi aiki da jikinta ta gaji sbd sun saba a lokacin ciwonta abu daya takeyi zuwa biyu ta gaji sosai ba kuzari. Body milk me kyau da qamshi ta shafa tareda Turare mai sanyin qamshi ta miqe ta nufi closet nata ta saka undies kafin ta saka oversize skirt and shirt na Liliana ta saka hula me laushi da rashin nauyi a kanta ta fito da slippers a kafarta sbd yunwa takeji abinci take buqata. Anty Anny ce ta nufo palon itama sanye da shaking doguwar riga mara adon komai sai kudi tana qamshi fuskanta fresh dan itama gaba daya yinin ranar bata fito daga bedroom ma bare palonsu harta fito zuwa nan sai yanzu data fito neman abincin da zata dan duk da a familyn kowa da nasa bangaren amma a hade suke guri daya babu wani rarrabewa sosai dan kusan duka a guri daya suke kowa baifi kayi tafiyar corridor ba zuwa palo da bedrooms wani hakama duk yanda kowa yake bangarensa a tare ake cin abinci dining room dinsu daya ne hakama chiefs dinsu da masu aikin. Rayuwar hutu kawai sukeyi mazan gidan ne suke fita aiki suma bawai sammakoba tinda sune masu companies dinsu amma matan kuwa da saleem ma sai lokacinda suka ga dama suke fitowa idanma ba abinci zasuci ba saika wuni a gidan bakaga ko dayansuba sai idan dare yayi ake taruwa babban palon ayita fira da yar hayaniya cikin walwala. Anny na ganin Jannah ta zuba mata idanuwanta tana kallan yanda take sake warwarewa tana komawa lafiyayyar jannah dinta wadda ita bata saniba a baya, Wani irin sirrin kyau da kwarjini ne da itama duk da bata gama zama cikakkiyar budurwar data amsa sunanta budurwanba amma haka kawai wani lokacin sai take mamakin saa irinta jannah din kowa sonta yake, Babu abinda ta nema ta rasa, Kowa zai iya komai dan bata abinda takeso, A irin wannan gatan da Jannah din take ciki me zata nema a duniyar nan ta rasa? Duk yanda familyn suke ganin babu abinda bazasu samar mata indai har tanaso akwai abinda yafi karfinsu shine ikon Allah, Ita kanta zataso Allah ya kawo abinda Jannah zataso fiyeda komai ko buqata fiyema da zuciyar da aka dauki rayuka da dama akanta amma kaf familyn babu wanda zai bata kuma dukiyarsu bazata taba iya siya musu ba, Zataso taga wannan ranar sedai batajin tana zuwa dan raine kadai bazasu iya siya mata amma ko rai din da zaace musu ana iya sakawa wani ran wani to tabbas zasu iya sedai Allah bai bada damar hakanba. Isowan Jannah gabanta ya sakata sake murmushi tana sake kallan Jannah da yanayi na tinani kala kala akan fatan zuwan ranar da jannah zata dandana rashin ba komai ake nema a samu ba. Da murmushi a fuskanta da kulawa tace "Hey Jan sai yanzu kike fitowa? Yaya jikinki? Ya kikeji yanzu? Karki manta duk abinda kikaji ba daidaiba ki sanar" Fararen idanuwanta ta kalli Anny din dasu kafin ta saukar da murmushin kwanciyar hankali a fuskanta tana cewa "Anty Anny karki damu i dont feel any uncomfortable yanayi, Am all good" Gaba tayi anty anny din na bin bayanta tana cewa "Masha Allah" Mimi ce itama ta fito a lokacin tana waya cikin walwala da annushuwa tabi bayansu dukansu dining room din suka nufa suka zauna daman dining din baa dauki mintina da yawa da gama shiryasa ba sbd ansan lokacin cin abincinsu na rana yayi kowane time zasu iya fitowa. Suna zama qamshin Ammar ya doso dakin me sanyi da tsadar gaske tareda rashin hawa kai ko kadan. Jannah ce taji wani sanyi yana ratsa xuciyarta tareda qamshin nasa ta dago idanuwanta tana kallan kofar daidai da shigowansa sanye cikin black thick riga da wando masu laushi fuskansa fresh da alama bai fita koina ba yau din shima yana gida hutu yake sosai haryanxu. Kyakkyawan fuskansa jannah take kalla tana jin bazaa samu namijin da zai kai Ammar Zad kyau da kwarjini tareda haiba ba a idanuwanta har abada ba, Ammar Zad shine mafi kyawun namiji data sani wanda shi kadai take zubawa ido bata gajiya da kalla. Kallan datake masa ya saka Anny sakin murmushi tana kallansa shima kallan Jannah din yayi yana sake murmushi yana kujera ya zauna yana cewa "Me Jan Zad take kalla?? Mimi ta kalla kafin ta kalli Anty Anny ta rage muryanta tace "The one and only Ya Ammar Zad" Mimi na jinsu farin ciki ya sake cikata tai sallama da wayarta ta kashe ta ajiye tana kallan Ammar din daya zauna kusa da ita yana daukan cup din fresh juice da akai na gida ya kai bakinsa yana cewa "Mimi barka da rana" Kafin ta amsa Jannah ma tace "Sannu da fitowa Mimi" Anny ma gaidata tai ta hada duka gaisuwar tasu tai musu amsawa daya tana cewa aci abincin tukuna wani zancen. ##MAMUH #JANNAH ZAD #AZIZ AY LIMBA #AMMAR ZAD #BESTLOVE STORY #CRAZYLOVE #BILLIONAIRES WAR ZAFAFA BIYAR KALBIM 500 mamuhgee A DUNIYATA 500 Huguma AJIYA A DUHU 500 Billyn Abdul KIRJIN ME HANKALI 500 Miss xoxo Pay at 0022419171 AccessBank Maryam sani gummi Shedan biya 09033181070 Or mtn vtu at 09032345899 [27/12/2024, 3:20 pm] MG: *_Arewabooks@Mamuhgee_* 28 *_LADIES COLLECTION AND MORE_* 08169307477 SHIN MATSALARKI RAMA CE KO KINA SO KI GYARA BREAST DINKI NE? KINA SO KIYI HIPS HAJIYATA KIYI KYAU? KO KUWA KINA SO KI RAGE KIBARKI KO TUMBINKI? KINA SON INGANTATTUN MAGANIN MATA NA GARGANIJIYA? Kinason shape dinki ya fito kamar yanda kowace mace zatai alfaharin ganinki bare ma oga ko saurayinki da kansa, Shin kinason ko koma yar dagwas dinki batareda kashe kudin surgery ba kokuma hana kanki cima da dama da kikeso sbd kinason jikinki yayi daidai? To matsalarki tazo karshe indai ingantattu sahihan maganin gargajiya ne da muka san inganci da gaskiyarsane, MAZA KI ZIYARCI LADYS COLLECTION AND MORE ko ta waya ko ta asalin inda take ki tabbatar da Buqatarki tazo inda zata biya insha Allah, LADY'S COLLECTION AND MORE ANAN NE ZAKI SAMU DUKKAN ABUBUWAN DA KIKE SO KAMAR HAKA 👇🏻 Zumar kiba Zumar breast Zumar hips Zumar infection Zumar sliming Zumar sabon budurci Back to virgin Abayas Atamfa Less Hijabs Supplements Kitchen items and more Muna maraba da masu siyan Daya ko 08169307477 Address bayan gidan drugs katsina State Kayan mu masu inganci ne sosae Muna aika kayanmu a ko Ina ba tare da wata matsala ba🙏🏻🙏🏻 SIYAN NA GARI MAIDA KUDI GIDA💯 *********** Da asuba jirginsu ya sauka Sayyid yana a sanyaye baida wani kuzari ko yin abinda ya wuce bin bayan Alh saad sawu kan sawu sbd kansa dayaji yana juyawa samun kansa a baqon guri inda bai taba tinanin zuwaba ko samun kansa ga jajayen fata tako ina suna wuce suna sake saka kansa juyawa amma ya daure babu abinda yake buqata irin ganin ABDULAZIZ LIMBA. Mota suka hau wadda kai tsaye takaisu train station suka siya ticket din zuwa Milan wanda acan ABDULAZIZ din yake. A train ma wata sabuwar duniyar Sayyid yake kalla wadda tale sake juyar da kansa sedai ko dagowa bayayi kansa na qasa Allah yasa kayan sanyi ne masu kyau da kauri a jikinsu dagashi har Alh saad dan haka rashin wayewansa da gurin ya boyu shi kuwa Alh Saad dayake gogagge ne a yawon qasashe sam babu abinda ya damesa sajewa ma yayi dasu banda banbancin fatar amma turancinsa dayakeyi hankali kwance cikin qwarewa yana waya da wanda zai kaisa har gidan ABDULAZIZ Tafiya sukai me dan tsayin data saka Alh saad jin daya sani flight suka sake bi zuwa milan din.. Suna sauka daga train Station daga nan kai tsaye motace ta daukesu zuwa Address din Fash wanda yake abokin karatun ABDULAZIZ tin abaya amma yanzu basa tare amma yasan sabon gurin dayake zama yanzu sbd dukkaninsu sun zama busy kowa ya samu success din dayake nema. Koda suka isa gidansa cikin sakewa ya tarbesu tareda riqesu sukai sallolin dasuke kansu sukai breakfast wanda daqyar Sayyid ya tura abincin a cikinsa sbd ba cimarsa bace hakama zuciyarsa kwata kwata a sanyaye take ba dadi ko kadan nauyi yakeji a kirjinsa. Wayar ABDULAZIZ din shima Fash ya ringa kira ko zaa dace amma still bata shiga ba kuma a lokacinda Alh saad ya kirasa baya qasar shima bai dade da dawowa ba dan haka bai samu zuwa ya dubo lfy ba kuma yayi masa gaisuwar babban rashin da yayi wanda duk wanda yasan ABDULAZIZ sanin daya wuce awanni to tabbas zaisan Ummitah itace rayuwarsa,jarumtarsa kuma karfin dayake riqe dashi a duk gwagwarmayar rayuwarsa hakama duk abinda yakeyi a rayuwarsa sbd cigabanta da ingatata yakeyi. Saida suka nutsu sosai kafin suka fito a motar fash din zuwa gidan ABDULAZIZ. Tin a mota sukai tsit babu me magana sai fash din dayake dan kokarin ragewa yanayin nasu damuwa da cewa "Insha Allah lafia kalau sbd LIMBA yana hakan so da dama idan yana son kadaicewa baya son damuwa" "Ummnh" kadai Alh Saad yace yana kallan hanya sbd baida abin fada. Sayyid kuwa shiru har lokacin bai iya cewa komaiba hakama ko kallan gari baida Nutsuwar yi. Shiru Fash yayi ganin yanayin baya buqatan karfafawa shiru kawai kowa yake buqata. Tafiyar mintina kusan 40 sukai kafin suka isa dogon building din da gidan ABDULAZIZ yake ciki. Parking fash yayi yana gaisawa da securities din wajen da suka bude musu hanyar shigowa fededen harabar gurin. Fitowa sukai dukkaninsu fash da Alh saad ne a gaba suna magana Sayyid dai har lokacin bai iya dago kansa sosai ba bayansu kawai yakebi a natse babu kuzari. Lift suka shiga zuwa saman Fash na daga wayarsa da ake kiransa. Suna isa floor din dayake suka fito fash yana kashe wayarsa suka tsaya kofa tareda sauke ajiyar zuciya ya miqa hannunsa ya danna Door bell dake qara mara damuwa da karfi. Kofar suka zubawa idanuwa dukkaninsu suna jiran fitowansa. Sake dannawa Fash yayi yana gyara tsayuwarsa. Shiru babu motsin alamar bude kofar, Sake dannawa Fash yaci gaba dayi yana shiga mamaki. Mintina suka dauka a gurin sunata bugawa babu alamar zaa bude din babu ma alamar akwai mutum a ciki. Saukowa qasa sukai suka nufi gurin receptionist din building din dake qasan Fash ne ya kalleta yana mata sannu kafin ya sanar da ita gurin wanda suka taho. Kallansu tayi dukkaninsu da mamaki kafin ta tsayar da kallanta kan fash da shine a gabanta tace "His family???? "Yes" yafada yana nuna su Alh saad din wanda shima Alh saad din matsowa yayi yana amsa gaisuwarta kafin tace "Baya nan for morethan 2 month yana asibiti likitansa yazo ya tafi dashi, Mutuwa yakeyi ciwo yake sosai....... Kallanta Alh saad yayi da sauri yana juyowa ya kalli Sayyid wanda bayajin abinda suke fada yana dan nesa kadan hakama turancin ba duka ya iyaba. Fash cikin Yanke zancen yace wane asibiti and the name of the doctor. Basu tayi cikin sauri sbd basuda tabbacin ko zuwa yanzu LIMBA din ya rasu sbd a yanda aka bar nan dashi batajin ko kwana daya zai qara a duniyar. *****A ranar kunnuwansa basu gama sauraron maganar Alh Saad ba yaji tsit bayajin komai jinsa na daukewa ahankali, Ganinsa ma Fara daukewa yayi qafafunsa ma mutuwa suka fara yi suna gaza daukansa hannuwansa da suka dauki rawa suma mutuwa suka farayi harsuna kashe wayar wadda ta zame daga hannunsa ahankali shida wayar suna zubewa agurin paralyse na kamasa a take. Buguwa kansa yayi da centetable din dayake tsakiyar palon take jini ya feso daga gefen fuskansa datai mugun buguwar idanuwansa da suka mummunan sauyawa a take na kafe akan wayarsa dake gaban fuskansa batareda ya kafta ba. Zuciyarsa kokarin dena bugawa takeyi sbd mummunan bugun datai wanda ya sakar masa paralys na take, Wani irin Radadin da baya misaltuwa ne yake ratsa zuciyarsa dake neman bugawa ta dena aiki gaba jininsa na gangarowa daga gefen goshinsa yana shiga har cikin idanuwansa da suka kafe akan waya bai iya motsa ko dan yatsantsa sbd babu abinda yake aiki ajikinsa bayan zuciyarsa datake matsanancin ciwo da radadinsa yake juyar masa da kai kafin ahankali idanuwansa suka rufe ruf ba alamar rai a jikinsa. A haka ya wuni a gurin kwance babu alamar rai a jikinsa harya kwana a gurin kwance babu taimakon kowa sbd babu wanda yake shigowa building din saida kwakwaran sanin gurin wa akazo hakama ko securities sun san shi kwata kwata baya wani muaamala da mutane hakama baya wani yawo sosai, A gurin kwance ya farfado sbd sanyin asuba dayake kadowa a hankali daga balcony dinsa dayake bude yana saukar masa.. Jajayen idanuwansa da ganinsu ya dauke ko kadan ya dena ganin komai ya bude suna wani irin radadin da duk azabarsu bayajin komai sbd har Allah ya dauki ransa dayake fata a yanxu bazai taba jin radadin dayake a yanzu yana yanka duk wani tsokar datake kirji da zuciyarsaba azabar daukan raine kadai da baisaniba yake jin zatafi abinda yakeji yana tarwatse zuciyarsa da kwakwalwansa datake dena aiki, A yanda yaken babu inda yake motsawa a jikinsa har gari yafara haske ya sake somewa a gurin sbd azaba da radadin dayake kirjinsa yayi masa tsananin da baya motsawa amma azabar tayi qarfin datake sumar dashi ya sake ficewa hayyacinsa. Mai aikinsu shida wanda yake next floor yazo aikinsa aikinsa guraren karfe 9 na safe kai tsaye ya bude kofar sbd yasan code na budewan. Iskan dayake kadowa daga balcony ne yana ratso palon me tsananin sanyin gaske ya saka Eden nufar hanyar balcony din bayan ya tafi extra room din dayake kaman nasa anan yake ajiye jakarsa da laptop dinsa ta karatu ko kallo ko wani abin idan yazo da ita. Sauke jakarsa yayi daga bayansa ya ajiye tareda ledar fresh fruits din dayazo dasu me girma wanda Tin jiyan LIMBA ya basa kudin ya siyo idan zai taho yau. Da ledar ya fito daga dakin ya nufi kitchen ya ajiye ledar ya nufo balcony din dan rufewa sbd sanyin yayi yawa sosai yana mamakin ya akai Mr LIMBA ya bar balcony din a bude sbd bayason sanyi sosai. Taku biyu yayi idanuwansa suka sauka akan LIMBA din dayake kwance a kife cikin mummunan yanayi ga jini a fuskansa duk ya bushe ba kyan gani babu alamar rai a jikinsa. Da gudun gaske ya nufesa cikin matsanancin tashin hankali da tsoro yana kiran sunansa. Birkitosa yayi da karfin gaske sbd nauyin da yay sosai alamar da gasken ba rai a tareda shi. Ihun gaske ya sake yana sakinsa ya miqe da sauri koina jikinsa na rawar tsoro da firgita, Kararrawan neman taimakon gaggawa zuwa ga securities da reception na building din ya danna da hannuwansa biyu yana sake daddanawa ba kakkautawa a rikice. Ganin kaman hakan bazaiyiba sai kawai ya rarumo wayar Limban datake gefe a yashe ta mutu ya nufi gurin caji da sauri yana kokarin sakawa manager da securities suka iso cikin sauri suna buga kofar ya bude da sauri yana jifa da wayar suka shigo da gaggawa suna ganinsa a hakan hankali tashe aka kira ambulance tareda likitansa dayake kamar Abokinsa Cikin gaggawa Dr Nico yace ayo asibiti dashi. A cikin nurses da suka taho da ambulance daukansa tin anan aka gane he is paralysed dan haka tin anan suka fara bawa rauninsa taimakon gaggawa aka kwashesa zuwa asibitin. A asibiti ana isa cikin gaggawa akai cikin emergency dashi sbd zuciyarsa dake bugawa ahankali kaman zata tsaya hakama numfashinsa dan haka hankalin dr Nico ya tashi dan suna buqatan gaggawar dawo da bugun zuciyarsa daidai idan ba hakan ba zaa iya rasashi. Kamar kar afara basa taimako ya rikice gaba daya kokarin rasashi akeyi dan haka hankalin likitocin gaba daya ya tashi aka saka masa oxygen ana kokarin hana zuciyarsa dena bugawa, Kokari sukeyi amma kwakwalwansa failing takeyi wanda kwata kwata baa son hakan... Duk yanda suka ringa kokarinsu babu abinda yake karban kokarin da sukeyi a jikinsa, Ba yanda suka iya dole aka yaga rigar jikinsa Dr Nico yace nurses su kawo Defibrillator Da gaggawa aka kawo tareda sauran abubuwan Dr Nico ya bawa dayar dr din shi ya fara hadawa da sauri Cikin sauri dr yace su kunna yafara kirga da sauri ya danna a kirjinsa ya basa AED a kirjinsa wanda ya sakasa yowan sama yana komawa ya zube babu alamar rai a tareda shi.. Da sauri ya sake cewa su basa wuta ya sake manna masa yana cewa "Com on com on com on LIMBA pls pls pls...... Cikin sauri nurse tace "hes Getting it Doctor" Cikeda fatan ya tashi ya hada na ukun yana danna masa sbd daga shi idan bai tashiba shikenan. Danna masa yayi yana daukewa Nurse tace "dr the heart..... Bata qarasa ba ya juyo da sauri yana cewa a basa sauran alluran da zai masa da gaggawa. Dr Nico ne yai masa alluran sbd bugun zuciyarsa ya dan samu karfi. Aden dayake wajen Emergency din yana kaida kawo cikin fargaba da rikicewa ya zauna ya tashi ya rasa ya zaiyi sbd tsananin Tausayin yanda A lokaci daya LIMBA ya koma kalar tausayi. Dr Nico damuwa ce sosai a tattare dashi sbd Bugun zuciyarsa ya dawo daidai sedai babu inda nasa yake motsi sun bincika sun tabbatarda ya samu paralys din da shock ne me girman gaske ya haifar masa dashi wanda zuciyarsa take kasa dauka. ##MAMUH #BESTLOVE #BROTHERS LOVE #RESTINPEACE UMMITAH LIMBA ZAFAFA BIYAR KALBIM 500 mamuhgee A DUNIYATA 500 Huguma AJIYA A DUHU 500 Billyn Abdul KIRJIN ME HANKALI 500 Miss xoxo Pay at 0022419171 AccessBank Maryam sani gummi Shedan biya 09033181070 Or mtn vtu at 09032345899 *_Arewabooks@Mamuhgee_* 29 *_LADIES COLLECTION AND MORE_* 08169307477 SHIN MATSALARKI RAMA CE KO KINA SO KI GYARA BREAST DINKI NE? KINA SO KIYI HIPS HAJIYATA KIYI KYAU? KO KUWA KINA SO KI RAGE KIBARKI KO TUMBINKI? KINA SON INGANTATTUN MAGANIN MATA NA GARGANIJIYA? Kinason shape dinki ya fito kamar yanda kowace mace zatai alfaharin ganinki bare ma oga ko saurayinki da kansa, Shin kinason ko koma yar dagwas dinki batareda kashe kudin surgery ba kokuma hana kanki cima da dama da kikeso sbd kinason jikinki yayi daidai? To matsalarki tazo karshe indai ingantattu sahihan maganin gargajiya ne da muka san inganci da gaskiyarsane, MAZA KI ZIYARCI LADYS COLLECTION AND MORE ko ta waya ko ta asalin inda take ki tabbatar da Buqatarki tazo inda zata biya insha Allah, LADY'S COLLECTION AND MORE ANAN NE ZAKI SAMU DUKKAN ABUBUWAN DA KIKE SO KAMAR HAKA 👇🏻 Zumar kiba Zumar breast Zumar hips Zumar infection Zumar sliming Zumar sabon budurci Back to virgin Abayas Atamfa Less Hijabs Supplements Kitchen items and more Muna maraba da masu siyan Daya ko 08169307477 Address bayan gidan drugs katsina State Kayan mu masu inganci ne sosae Muna aika kayanmu a ko Ina ba tare da wata matsala ba🙏🏻🙏🏻 SIYAN NA GARI MAIDA KUDI GIDA💯 *********** Duk yanda Dr Nico ya dage sosai cikin tsananin tausayawa yana neman lafiyar LIMBA sam babu cigaba sbd baya karban treatment da ake basa sbd Zuciyarsa data riqe da abinda yake cikinta sai sauki baya samuwa, A kwance yake ba motsi ba magana ba kuka ba kowane irin reaction da ake samu daga garesa dan haka jikin nasa yake sake mutuwa, Manyan likitocin da sukeda su asibitin Dr Nico ya sako a case din ABDULAZIZ suka duqufa amma sam sbd bayason ya tashi duniyar yakeson bari shima sai babu sauki a zuciyarsa ko sassaucin tsananin quncin dayake cikinta sai anata magani amma ba sauki. Aden ne yake kulawa dashi sbd ABDULAZIZ yayi masa abinda baitaba samu daga kowa ba, Shine ya dauki nauyin karatunsa dana kanwarsa sbd duk inda yaga yaya yana son kanwarsa jin yake yana kauna da Tausayinsu dan haka babu abinda bazai iya yiwa ABDULAZIZ LIMBA ba dan haka yake jinyarsa. ****lokaci yafara tafiya babu wani sauyi daga lafiyarsa, Wata rama yakeyi sosai tana cinyesa daga kwance tana busar da fatarsa, Ya tara suma da gashin fuskan har lokacin babu abinda yake motsi a jikinsa, Asalin qunci da radadin da babu magani ne yake cin zuciya da ruhinsa ko idanuwansa bai cika budewa a rufe suke kusan koyaushe sbd basuda kyan gani suma sun kode sun jeme radadi da qunci kawai kake hangowa a cikinsu tareda cire rai daga duniya da abinda duka yake cikinta. Aden ne ke dawainiya dashi komai shine yake masa cikin kulawa da fatan samun lafiyansa gashi duk yanda zasuyi contacting familynsa an rasa sbd wayarsa ya rasa inda ya yarda ita an nema an rasa dan haka suke dawainiya dashi shida dr nico wanda yayi iya kokarinsa akan ABDULAZIZ ya sassautawa zuciyarsa dan saiya sassautawa kansa zasu samu lafiyar da ake nema masa tafara samuwa amma hakan baya samuwa dan haka ya hakura yana cigaba da kulawa dashi sedai ahakan ya sani ABDULAZIZ bazai dade a duniyarba zai iya samun bugawan zuciya daga kwancen. ***Aden ya sadaukar da rayuwarsa a watannin akan ABDULAZIZ din wanda suka hakura suka cire rai daga tashinsa sbd ya koma ba kyan gani Ahankali ahankali yake rasa sauran ji da ganin daya rage masa.... Kuka sosai Aden yakeyi a lokaci da dama idan ya kalli ABDULAZIZ din idan ya tina asalin kamanninsa da haibarsa tareda wani irin aji da kwarjininsa tareda tsarin rayuwarsa datake cike da Class da burgewa amma ayau gashi a kwance komai sai anmasa. Ahakan ya dauki watanni koyaushe suna jiran ji daga familynsa tinda su sun kasa samunsu. ************* Motar fash ce tayi parking a asibitin cikin damuwa da shakkar halinda ABDULAZIZ din yake ciki suka qarasa reception suka fadawa nurse din dasuka samu agurin cewa Dr Nicolas sukeson gani. Kallansu tayi kafin tace dr Nicolas din ya shiga tiyata sedai su jira. Kallanta Alh saad yayi yana cewa "akwai patient me suna ABDULAZIZ LIMBA mune familynsa" Kallansa tayi kafin ta kalli Fash da shima itama yake kalla yana jiran amsarta. Dawo da kallanta tayi kan Alh Saad tana mamakin lokacinda suka dauka basu taho garesa ba duk mummunan halin dayake ciki baida jininsa a kusa. Numfashi me sanyi ta sauke tana cewa "AZIZ AY LIMBA????? yes" suka ce mata dukkaninsu cikin sauri. Kallan nurse din kusa da ita tayi ta fada mata familyn Patient din dr Nicolas ne LIMBA. Itama nurse din kallansu tayi d sauri tana ajiye Wayar datake amsawa da mamaki tace amma basusan halinda yake ciki ba ko? Yes sukace suna cewa ganinsu kawai suke tsananin so a yanzu. Room number aka fada musu bayan an duba id cards nasu an dauki sunan da sauran bayanai se dayar nurse din datake kulawa dashi wani lokacin cewa tai su biyota takaisu. Bin bayanta sukai Banda Fash da akaiwa kiran gaggawa kuma mahaifiyarsa ce dan haka su kadai suka nufi dakin ya juya da niyar zai dawo anjima. Tinda suka kama hanyar dakin dayake bugun zuciyar Sayyid ya tsananta yana jin jikinsa na sanyi yana jin ciwon lokacinda suka dauka batareda an taho duba lafiya ba jinsa shiru wanda da Ummitah na raye bazata ji dadin hakanba.... A kofar dakin nurse ta tsaya tareda nuna musu su shiga ta juya tabar gurin zuwa aikin gabanta.. Alh Saad ne ya miqa hannunsa ya bude dakin tareda turawa ya shiga kai tsaye yana Jefa idanuwansa Ko taku biyu baiba ya tsaya cak yana kallan Abinda yake gabansa cikin wani irin tashin hankali da tsoro zuciyarsa na cika da tsoron Allah mai tsananin gaske na ganin ABDULAZIZ yanda koma dan ma kasa gasgata idanuwansa yayi ya juyo da sauri ya kalli Sayyid wanda ya kasa qara taku ko daya daga inda yake yana kallan Hamman Ummitah wanda yake zaune kan kujera an dauresa sa belt sbd baya iya zama kamanninsa kaf sun sunya zuwa wani quncin da kansa, Tea me kauri Aden ke basa amma baya shiga dawowa yakeyi yana saka tissue me yawa yana goge masa..... Wani irin kukan dayake tafe da tsananin qunci da radadin zuciya ya kufcewa Sayyid yana tahowa da sauri ya rungume ABDULAZIZ din wanda ya rintse jajayen jemammun idanuwansa a karon farko hawaye masu tsananin dumi na biyowa gefen idanuwansa suna gangarowa. Kuka sosai Sayyid keyi yana jijjiga ABDULAZIZ din zuciyarsa na radadin dayake jinsa har cikin kansa yana kasa cewa komai, Kukansa ne yake ratsa zuciyar ABDULAZIZ da babu komai a cikinta empty take yana zana masa mutuwar yar uwarsa a zuciyar.... Zuciyarsa Alh saad ma kasa riqe jarumta yayi hawayene suke gangaro masa yana kallan hawayen dake gangarowa gefen idon ABDULAZIZ idanuwan a rufe. Tsit dakin yayi kukan Sayyid me wani irin ciwo ne ke ratsa dakin cikin sauti me ratsa zuciya da sake dawo musu da mutuwar sabuwa. Aden ma kukan yakeyi sbd ganin se yau hawaye ya sauko daga idanuwan ABDULAZIZ wanda zafinsu yake tabbatar da tsananin radadi da ciwon dayake zuciyarsa. Sun jima a wannan yanayin me kashe jiki da quncin daya dawowa kowa sabo sai ga dr Nicolas daya taho da sauri jin familyn LIMBA din sun zo. Hawayen daya tarar sun sauko daga idon ABDULAZIZ ya sakasa jin wani relief sbd zuciyarsa ta fara dawowa da feelings din daya rasa. Kallansu yayi yaga irin yanda Sayyid ke kuka idanuwansa sunyi jajir ya dawo sa kallansa akan Alh Saad suka gaisa yana musu barka da zuwa tareda fara masa bayani akan ciwon nasa. Numfashi me zafi Alh saad ya sauke tareda yiwa dr din godia mai tsananin gaske kafin ya kalli ABDULAZIZ din wanda idanuwansa suke rife yafara fadawa dr din qanwarsa ce ta rasu gurin haihuwa.. A kunnuwansa yakejin Ana fadar rasuwar Ummitah amma baya iya ko motsawa bare nuna quncinsa dan ya sake rintse idanuwansa radadin kirjinsa na qaruwa wasu sabbin hawayen suka sake gangaro masa yana jin karban ciwo da radadin da zuciyarsa ke masa. Rasuwar Ummitah ta girgiza dr Nico din sbd yasan kaunar da limba kewa sister dinsa wanda kaunarta kamar dabiace kokuka ace kamar sunansa ne dayake yawo dashi dan haka ya tausayawa ABDULAZIZ tareda tabbatar musu da insha Allah Zai warke amma saiya bawa zuciyarta sassauci. Duk yanda sukaso magana da ABDULAZIZ babu damar hakan sbd dai ba alamar ma yanaji din duk da yana jin amma basusan da hakan ba, Sayyid sunkuyar da kansa yayi a gaban ABDULAZIZ daya kasa tashi ciwo kirjinsa yake masa mai tsananin gaske na ganin ABDULAZIZ hakan. Shi kansa ABDULAZIZ din bai bude idanuwansa ya kallesaba tinda ya rufe dan haka a haka sukai shiru babu wanda ransa ba cike yake da damuwa da qunciba.. Aden ne ya fita dakin ya basu guri bayan ya qarasa goge masa jikinsa. A asibitin suka wuni sai dare Aden ya tafi dasu gidan ABDULAZIZ din wanda yake fes cikin tsari me kyau da jin dadin rayuwa. Alh Saad Sayyid kawai ya bari a gidan wani lafiyayyan lodge ya sauka sbd bazai yiyu ya zauna gidan ABDULAZIZ dinba sbd komai na ABDULAZIZ din akan tsari yake hakama ya wuce wani ya zauna gidansa sbd privacy nasa amma Sayyid qaninsa ne ba damuwa bane. Shi kansa Sayyid bayan tafiyar Alh saad kasa zama yayi yafadawa Aden shima zai bisa ya kwana asibitin. Dayake basa wani gane zancen juna amma ya gane dan haka bai musa masa ba suka koma tare. A asibitin a wannan daren Sayyid ne yake kamawa Aden kulawa da ABDULAZIZ wanda tinda suka taho bai sake bude idanuwansaba. Washe gari Alh saad yazo ya sake tattaunawa da Dr Nico akan ciwon. Sayyid kuwa hankali ya maida kawai akan lura da komai na kulawa da Hamman sbd ya karbi kulawan dashi da kansa. A ranar ma a asibitin Sayyid ya kwana tareda aden sai gashi cikin kwanaki kadan ya karbi ragamar kulawa da ABDULAZIZ din Aden ya samu ya maida hankali akan karatunsa. ****Sabon treatment aka fara yiwa ABDULAZIZ LIMBA wanda shima sam baya karba amma dagewan Sayyid daya fara taimakawa gurin dawo masa sa emotions dinsa da zancen Ummitah da fada masa yanda tayi rayuwa a kwanakin datake gaf da barin duniya da irin ciwon data ringa ahankali da yanda take maganarsa sai hakan yake motsasa hawayensa masu tsananin radadi koyaushe cikin gangarowa suke daga idanuwansa. Kusan wata daya Alh saad ya share a garin anata fama kafin yafara shirye shiyen tafiya bayan an sallamo ABDULAZIZ din sunso dawowa Nigeria dashi doctors suka bada shawarar kada ai hakan su bari ayi treating nasa anan dan haka dole yabarsa tareda Sayyid wanda gaba daya ya koma baida hidima saita ABDULAZIZ din wanda ko idanuwansa bai cika budewa. Bayan tafiyar Alh saad Aden ya dawo gidan sbd Fita siyayyar abubuwan buqatan gidan da sauran abubuwan da sayyid bai saniba shi kuma Sayyid rayuwarsa ta koma ABDULAZIZ kawai. ****jinya sukeyi me wahala sbd babu alamar sauki har lokacin hakama shi kansa Sayyid din ya koma kalar tausayi sbd yanzu wani lokacin idan trauma din ABDULAZIZ din ta tashi haka zai rintse idanuwansa ya wuni ya kwana bai budesu ba hawayene kawai ke fitowa acikinsu suna gangarowa masu zafi.. A duk lokacinda ya shiga wannan halin Sayyid damuwa yake shiga sosai idanuwansa suyi jajir sbd shi a zuwa lokacin zuciyarsa ta fara bushewa sam baida wasu emotions din yakeji shima. Lokaci yafara tafiya kwatsam saiga Alh saad da mama da baby fatima ya kawosu sbd Mama dake neman mutuwa itama da damuwa da kunci ga jaririyar da takasa bawa anty maryam kuma ita bazata iyaba sosai sbd ciwo da manyanci dan haka ta koyaushe rokonta yakaita taga ABDULAZIZ kafin tabar duniya hakama akai masa 'yarsa yagani kila ya samu qwarin gwiwan da aketa son ya samu. Zuwan mama da baby fatima ya qarasa rikita jikin ABDULAZIZ din gaba daya wanda komai ya dawo musu baya sedai kuma a ranar da aka ajiye masa Baby fatiman a kan jikinsa har an cire rai daga samunsa sai gashi Allah yasa yanada sauran kwana gaba dan haka likitoci suka ce a ringa kowota gabansa koyaushe. Alh Saad ganin rayuwar Sayyid na neman mutuwa ya saka ya yanke shawarar sakasa makaranta yafara zuwa yana kulawa da ABDULAZIZ kuma dan haka ya zama baida ma lokacin kansa koyaushe busy yake. Mama ganin ABDULAZIZ yasaka nata ciwon warkewa dan haka da ita suke jinyar abinsu wanda cikin ikon Allah aka fara samun yanda akeso sedai babu alamar zai taba komawa ABDULAZIZ dinsa na baya idan ya miqe. #MAMUH #THE NEW AZIZ LIMBA ZAFAFA BIYAR KALBIM 500 mamuhgee A DUNIYATA 500 Huguma AJIYA A DUHU 500 Billyn Abdul KIRJIN ME HANKALI 500 Miss xoxo Pay at 0022419171 AccessBank Maryam sani gummi Shedan biya 09033181070 Or mtn vtu at 09032345899*_Arewabooks@Mamuhgee_* 30 *ZUZEAM VENTURES* Best APHRODISIAC 08144015291 Aslm barkanmu da wannan lokaci Ina Mai farin cikin sanar daku cewa Zuzeam ventures takawo maku ingantattun magunguna masu inganci cikin Aminci Muna da kaya kamar haka Mallaka Maganin sanyi Maganin cire tumbiMaganin farin jini Maganin matsiMaganin mata Maganin sa ni’ima da dandano Dulka Amare Set na gyran jiki Set na amarya Tabaje tsumin Gomba Xuma kiba ta hips and Brest Magungunan gyran Brest Magungunan Karin hips Maganin sliming Muna da kaya masu inganci cikin sauki da rahusa Ina wadda keneman mallaka sahihiya quaranty wlh hajiya kixo ga zuzeam ventures xakiji ddin mallaka duk fadin ran ogah duk fadansa wlh sai yyi sanyi 08144015291 Idan maganin mata kikeso akwai Idan gyran jiki kikeso gyran fata gyran Brest magungunan sa kiba da hips DOMIN samunta Kai tsaye kira wannan no 08144015291 DOMIN mgn da ita whatapp 08144015291muna tura kayanmu ko ina cikin iKon allah 🥰👌🏻 Bononza Bononza Tsimin mangoro 1k🥭 Tsimin dabino 1k Gumba ukku balai 700 Gumba aya da nonon rakumi 700 Garin kafi ciccibi 500 Garin bata gaban kishiya 500 Matsin mallaka tada zaune tsaye 2500 Turaren mallaka ba aba mai kishiya 2500 Total kayan 9500 Za a bakisu akan 3800 Kuma mutun goman farko nadakyautar Abun 2k 🗣️🗣️🗣️🗣️🗣️🗣️ ASSALAMU ALAIKUM ALHAMDULILLAH YAN UWA NEW PROMO YA KAMMALA💃🏽💃🏽💃🏽😁😁😁 da 5k dinki ki kwashi kayan 12k hajiyata 💃🏽💃🏽💃🏽😃🙃Kazar gadali ta mallara Rabi 3500 Tsimin gam gam 1500 Ruwan kara zunzurutun dadı😋800 Garin 7in1 1k Gumba 3 balai 500 Gumba kwakwa da dabino 500 Infection ruwan tsarki 1k Garin zunzurutun dadi 1200 Matsin ba a fira d wando 500 Matsin infection mai matse mace gam 500 12k All at 5k kedai dannan link dinnan don samun naki ki maza kiyi bucking koda kudinki saida Rabonki ************* Baby Fatima ce ta zamo sabuwar hasken idaniyar data farfado da rayuwarsa daga mutuwar datake wadda baitaba fatar ya tashi ba, Fatarsa Allah ya dauki rayuwarsa batareda ya warke ba sedai a duk lokacinda ya kalli Fuskan babyn data dauko kamminsa da mamanta fuskan Ummitah yake gani a cikin tata dan haka ta zama hasken zuciya da rayuwarsa da bazai iya ba dan haka tinda tasa kaddarar ahakan tazo itama zai reneta kamar mahaifiyarta ya inganta rayuwarta ya bata gatan da tarbiyar da zata rage masa filin da Ummitah tabar masa dan har abada wannan filin bazai taba cikewaba harya bar duniya sbd Ummitah itace rabin ABDULAZIZ AYOUB LIMBA kuma ta tafi dan haka ta tafi da dukkanin emotions da feelings nasa babu abinda ya rage masa bayan fili a zuciya. Lokaci na tafiya lafiya tana samuwa garesa amma duk wannan lokacin bai taba bude bakinsa yayi magana suma tin suna jiran maganarsa har suka hakura suna fatar samun lafiyansa tukuna. A ranar daya fara karban baby fatima da hannuwansa biyu a ranar ne ya bude bakinsa ya fasa wani irin kuka mara sautin daya girgiza mama da sayyid suka shiga tashin hankali gidan yayi tsit a ranar babu wanda ko ruwan gidan yasha da dadin zuciya daci da qunci ne ya cike koina na cikin gidan har dare bai fitoba. Ranar a gurinsa Baby fatiman ta kwana wadda itama tafara sabo dashi dan bataima wayon sanin waye babanta a tsakaninsu ba duk da Sayyid ya sadaukar nuna mata yakeyi ABDULAZIZ dinne mahaifinta tinda tafara wayo da girma sbd shekara biyu cikin ta uku ake magana. ******Sayyid da rayuwarsa sun sauya sosai acikin shekarun sbd dawainiya da zamowa kaman shine shugaba a familyn yanzu hakama ga huldodin ABDULAZIZ da abokan aikinsa suke tafiyar dasu sosai shine mai bibiyarsu tin bai sababa harya saba ga karatunsa dayake masa wuya sbd rashin qarfin turancinsa ahaka yayita fama harya tsayu ya zama dan qasa ya goge ya wanke ya koma SAYD yanda suke kiransa, Mama ta dade da dawowa hayyacinta sbd ganin zasu rasa ABDULAZIZ dan haka ta miqe tsaye sukai gwagwarmaya harya dawo kan kafafunsa y dawo ABDULAZIZ wanda ya tashi daga wanda suka sani, Tinda ya warke bai taba bude bakinsa yai maganar rasuwar Ummitah ba suma sbd gudun janyo masa wani radadin dayake kokarin boyesa aransa yasa basu tada maganar komaiba sbd tin yana ciwo Sayyid yasha fada masa yanda ta rasu da inda take a rufe da janazah da akai da komai. Bai fara fita aiki ba bare yawon business a gida yake aikinsa da laptop irinsu conference calls da meetings da sauransu. Jinyarsa bata saka arzikinsa baya ba sbd babu abinda ya tsaya a ciwonsa cigaba akai da business kawai dan haka arzikin yanzu yake take na bayan dan haka yafara kokarin fitowa karban ragamar komai tareda sayyid daya goge a harkan business da computer daya yiwa karatun qurulla sbd kusan maye ne shi akan duk abinda ya sakawa ran sani dan haka yake kamar wani maye akan karatunsa da aikin da duk ya shafi ABDULAZIZ LIMBA. **FALAQ AZIZ LIMBA shine Sunan dayake kiran 'yarsa yar kamannin shekara 6 zuwa 7 wadda ta taso cikin gatan daya wuce misali hakama batasan tanada wani ubanba a duniya kaf bayan Daddyn nata wanda take cewa BESTDADDY, ***Sayd ya zama cikakken matashin dayake ji da Ilimi da tsari tareda da Zama final say din AZIZ AY LIMBA sbd zamansa personal person dinsa., A lokacinda baby Falak ta cika shekara bakwai a lokacin suka bar italy suka koma United States Sbd sabuwar duniyar datazowa ABDULAZIZ LIMBA ta wani irin kudin dayake tashensu wanda yake zamowa abokin manyan mutane dake ruling qasashe masu powers da iko, Sayd sake kutsawa yayi a cikin karatun dayake sake sauya rayuwarsa gabaki daya yana komawa kaman black American, Mama ma rayuwarta haka ta koma kamar batai zaman Nigeria ba dan hutu da kwanciyar hankali ya ratsata tareda da wata irin daula da asalin abinda ake cewa arziki. Falak itace abu daya da duk duniyar the great AZIZ AY LIMBA baya wasa da lamarinta dan kuwa ko yawan tafiye tafiyensa ita kadaice takeda iko da damar kiransa aduk lokacinda taga dama koda yana tareda mutane masu mahimmanci baya qin daga wayarta gashi sam bata taba normal call dashi ba idan ba vidcall ba dan haka kusan duk abokan businesses nasa sunsan baida kamar 'yarsa tal kuma sun san baya hadata da komai. Kaf duniyarsa idan ba daidaiku Nigeria ba basu taba sanin ba shine asalin mahaifinta ba kaman yanda itama bata saniba saninta Sayd Uncle nata ne dayake tsananin sonta shima hakama itama tana tsananin sonsa. Babu aure a gabansa dan bai taba tinaninsa ba bare kallan macen ma da zai iya auren duk da yayan manyan anyita son hada family dashi hakama abokan businesses nasa sunata son hada family dashi sedai bai shirya hakanba kwata kwata,babu tsarin hakan a rayuwarsa 'yarsa ta ishesa rayuwara. *********** Shekarun da suka wuce da yawa ba iya Familyn LIMBA suka sauyaba da samun sabuwar rayuwar har mutane da yawa da duniyarma kanta abubuwan suna sauyawane da tafiyar kwanaki zuwa shekaru, Yara qananu sun girma sun zama yan mata,wainda baa haifaba ma an haifa,wainda basuyi aureba sunyi sun hayayyafa, Wasu sun samu ci gaba wasu sun samu ci baya, Wasu sun bar duniyar ma hakama wasu suna nan yanda suke saidai tsufa dayake zuwa kaman yanda damuna da rani suke tahowa suna wuce komai ya sauya a koina na rayuwar da duniyar. JANNAH ZAD ta samu sauyin rayuwar datake cike tattare da cigaba daya zarce na komai a rayuwarta ta baya data zama tarihi gareta da duk ahalinta, Iyayenta sun turata qasar datake burin karatu ta samo ilimin da ciwo ya hanata samu, Rayuwarta tana cikin haske da cigaba tareda kwanciyar hankali da walwalwa me tarin yawa musamman sbd tana tareda Ammar dinta wanda yake tamkar kariya agareta sbd checkups nata da baya wasa dasu sbd rayuwarta zata qarasate ne akan checkups da baa denawa lokaci lokaci, Rayuwarta ta sauya,kamanni da halaye da jiki da dabiu da komai nata ya sauya daga Zeynab zuwa beautiful classy Jannah Zad wadda take tashen Kyan jiki da fuska dana zuciyarta data banbanta sosai data ahalinta, Akwai kauna mai karfi da tsafta datake ji a tsakaninta da zuciyar datake bugawa a kirjinta wanda lokuta da dama takanji kadaici yana tsananin rufeta da kewan mai zuciyar wanda haryanzu batasan waye ya bata ba kuma waye familyn sbd su Dad kwata kwata sun sanar da ita wanda ya bata najimi ne kuma bama a Nigeria yake ba baida kowa maraya ne daga ghana aka samo. Da wannan aka hanata neman koda familynsa ne sedai tanajin akwai kauna sosai tsakaninta dashi wanda ko sunansa bata saniba amma babu ranar da bata masa adduar samun rahamar ubangiji a makwancinsa. Ammar Zad shine wanda zuciyarta take tsananin so bayan iyayenta da kuma kauna ta yan uwanta So ne mai karfi a tsakaninsu. Ammar son dayake mata ya take wanda take masa sedai yana samun kansa a cikin matsanancin rudani da yawan lokuta sbd Soyayyar datake masa tafi kama data jini hakama hakanan yake jin koyaushe kaman bata gama zama tasa ba a zuciyarta da kwata kwata basa gane wane irin so takewa abu, Amma dai ko yayane tinda tana son nasa bayada burin daya wuce hakan aure kuma basa buqatan rushing abubuwa sbd a yanzu ta samu cikakkiyar lafiya samun iliminta shine komai zatai karatu ta zama cikakkiyar macenta a yanda take yanzu kafin komai. Familynta na cikin farin ciki da walwalwan dayafi na baya sbd samun lafiyarta komai ya daidaita a familyn Suna komai na businesses nasu cikin cigaba da samun daukaka da kwanciyar hankali, Basu bar Nigeria ba tinda suka dawo sedai Dr Abraham dasuka koma qasarsu duk da sun sabu da Nigeria din amma suna yawa zuwa inda sbd har koyaushe dr Abraham ya riga ya zama kamar shine me asibitin amma zadeens kuwa kwata kwata zuwa asibitin ya zama shafaffen tarihi garesu tin daga lokacin dan ko ciwo dayansu yayi gida doctors ke zuwa dubasu. Duk wanda yasan zaadens yasan zaratan Mazan dake familyn masu ji da lokaci da aji tareda tsagwaron ilimi da aji, MAHEER ZAD ya zama kamar babban mutum dayake hulda acikim manyan mutanen dasuka haifes a matsayin abokan business dan duk abokan business din iyayensa Sun zama nasa abokan dashi ake huldan da duk zaa iya yi da Dad dinsa ko Daddy mahmoud dan haka matsayinsa da Karfinsa yayi girman da girmamawan da ake bawa iyayensa ita ake basa a gurin mutane da abokan business, A gida kuwa Matarsa ta samu duk duniyar datake mafarki da burin samu harma ta wuce dan kuwa rayuwar iko da daular da bata jin barna take dan haka ta zama cikakkiyar Zad itama daman a zuciya ma daya suke. AMMAR ZAD kuwa rayuwa biyu yake juyawa ta zamansa Zad da zamansa likata me zaman kansa da duniya bata saniba amma dai businesses din iyayensu shima yake ciki sosai, Duk wani lissafin tarin kadarori da uban dukiyar da suke da ita shine yake gudanar da komai sai bangare daya bai cika zama ba yana hanyar zuwa gurin Jannah wadda take Cyprus tana karatu tareda a gidan Daddy mahmoud wanda yake jiran ta gama shima su tattaro su dawo Nigeria gaba dayansu. Ammar kusan yafi su Maheer kyau da daukan ido sbd Mum dinsa ya dauko gaba daya wadda tafi yayunta kyau duk da kusan duk kamanninsu daya dan haka Jannah take ganin a idonta babu wanda zai kai Ammar Zad dinta kyau da aji da kamewa dan bata taba sanin yanada trauma ba duk wannan abin da ake sbd idan ta taso masa sam bayada kyan gani. Amma koda ta sanin a yanda yake a ranta zata iya sonsa a hakan batareda wani second tinani ba... SALEEM ZAD shine me zafin cikinsu da baya cika shiga zabgar family business din yanada nasa business na kamfanin saida motocinsa daya bude wanda yake gudanarwa amma dai duka da sunan familyn ne wanda daima kamar family business dinne ya bude musu sabo kuma hakan yana tafiya fiyeda tsammaninsu dan haka sukai investing mugayen kudi akan business din kamfanin motocin sedai Akwai wani shegen daya zarce tinaninsu akan business din na motocin wanda Saleem Zad ke tsananin burin aiki dashi sedai hakan ya kasa samuwa amma yana kokari akan hakan. Mimi Zad kuwa hankalinta kwance yake tinda ahalinta suna cikin Aminci da kwanciyar hankali kowa na samun yanda yake so dan haka ita hakan shine farin ciki da burinta sai kuma Auren Ammar da Jannah datake fatan Allah ya nuna musu anyi sbd hakanan takejin batada Nutsuwa idan baai aurenba kaman bazaayi ba take gani wanda tasan Ammar na rasa Jannah komai zai iya faruwa dashi sbd son dayake mata ya hadu da trauman datake damunsa ya zama kamar possession. DZAD da DADDY MAHMOUD kuwa duniya tayi musu duk yanda sukeso sbd suna juya rayuwa yanda suke sonta, Allah ya basu power da duk abinda suke so a rayuwar dan haka basuda matsalar komai sai rayuwa yanda sukeso suda iyalansu. ##MAMUH #JANNAH ZAD #AY LIMBA #AMMAR ZAD #FALAQ LIMBA #SAYD LIMBA #ZAADENS ZAFAFA BIYAR KALBIM 500 mamuhgee A DUNIYATA 500 Huguma AJIYA A DUHU 500 Billyn Abdul KIRJIN ME HANKALI 500 Miss xoxo Pay at 0022419171 AccessBank Maryam sani gummi Shedan biya 09033181070 Or mtn vtu at 09032345899*_Arewabooks@Mamuhgee_* 31 *ZUZEAM VENTURES* Best APHRODISIAC 08144015291 Aslm barkanmu da wannan lokaci Ina Mai farin cikin sanar daku cewa Zuzeam ventures takawo maku ingantattun magunguna masu inganci cikin Aminci Muna da kaya kamar haka Mallaka Maganin sanyi Maganin cire tumbiMaganin farin jini Maganin matsiMaganin mata Maganin sa ni’ima da dandano Dulka Amare Set na gyran jiki Set na amarya Tabaje tsumin Gomba Xuma kiba ta hips and Brest Magungunan gyran Brest Magungunan Karin hips Maganin sliming Muna da kaya masu inganci  cikin sauki da rahusa Ina wadda keneman mallaka sahihiya quaranty wlh hajiya kixo ga zuzeam ventures xakiji ddin mallaka duk fadin ran ogah duk fadansa wlh sai yyi sanyi 08144015291 Idan maganin mata kikeso akwai Idan gyran jiki kikeso gyran fata gyran Brest magungunan sa kiba da hips DOMIN samunta Kai tsaye kira wannan no 08144015291 DOMIN mgn da ita whatapp 08144015291muna tura kayanmu ko ina cikin iKon allah 🥰👌🏻 Bononza Bononza Tsimin mangoro 1k🥭 Tsimin dabino 1k Gumba ukku balai 700 Gumba aya da nonon rakumi 700 Garin kafi ciccibi 500 Garin bata gaban kishiya 500 Matsin mallaka tada zaune tsaye 2500 Turaren mallaka ba aba mai kishiya 2500 Total kayan 9500 Za a bakisu akan 3800 Kuma mutun goman farko nadakyautar Abun 2k 🗣️🗣️🗣️🗣️🗣️🗣️ ASSALAMU ALAIKUM ALHAMDULILLAH YAN UWA  NEW PROMO YA KAMMALA💃🏽💃🏽💃🏽😁😁😁 da 5k dinki ki kwashi kayan 12k hajiyata 💃🏽💃🏽💃🏽😃🙃Kazar gadali ta mallara Rabi 3500 Tsimin gam gam 1500 Ruwan kara zunzurutun dadı😋800 Garin 7in1 1k Gumba 3 balai 500 Gumba kwakwa da dabino 500 Infection ruwan tsarki 1k Garin zunzurutun dadi 1200 Matsin ba a fira d wando 500 Matsin infection mai matse mace gam 500 12k All at 5k kedai dannan link dinnan don samun naki ki maza kiyi bucking koda kudinki saida Rabonki ********** December 2024 Starling City US Fresgills No 124 LIMBAs Res Fiddausirwl me dan girma a hannunta ta nufi dining room tana dan kallan time na agogon dayake hannunta ta kalli hanyar dakin Falaq dayake hanya daya da dakin Daddynta Dayake gari dan hakan ne ya saka gidan yau ba doguwa hayaniya gurin aiki sbd matiqar yana nan hutun gaske yake buqata Sayd yasha fada musu doka ce ba wai kaida ba dole ne ayi maintaining kai. Dining ta shirya tsaf wanda yakeda girma ta gama jera duk wani abinda tasan Sir AZIZ AY LIMBA yana ci a breakfast dinsa dana falaq wadda gata yayiwa wani irin kamu kwata kwata, Sai kuma abinda Sayd shima yake cimarsa Mama kuwa yawanci breakfast dinta kome zata ci batada damuwa amma sai an hada mata da kunun Gyada dayake kamarma na madara zalla. Tana gama shirya Dining ta koma kitchen ta kalli sauran masu aikin biyu ta tinatar dasu nan da awa biyu zaa fara shirin abincin lunch na gidan duk da sun tsani sbd sun dauki shekaru a gidan suna aiki amma kaidarta ne ita kuma tina musu koyaushe sbd a yanzu ta yawanci umarni ne nata sai kulawa da Falaq wadda yake asalin aikinta me mahimmanci kenan. Fitowa tai daga kitchen din ta nufo lafiyayyan palon gidan dayake tashin wani lafiyayyan qamshi me hade da sanyin aircon daya kama koina, Dukiya ce take magana koina a gidan sbd luxuries ne koina na waiga a gidan yake magana da class tareda rashin hayaniya da kwanciyar hankali. Hanyar dakin Mama tafara nufa ta bude palonta ta shiga shima qamshi ne da sanyin ac ke tashi me dadi yana sanyaya jiki da zuciya. Kai tsaye Bedroom dinta ta nufa tana sake duba ogogonta sbd lokacin tashin Falaq datake jira sbd yau weekend ne ba school amma zata tafi school campaign da zaayi na yara dan haka tasan saita lura sosai batareda ta qara ko wuce time da zaiyi daidai da fitowar daddynta ba. Ahankali cikin nutsuwa ta miqa hannunta tai knocking kofar bedroom din kafin ta bude tareda sallama a bakinta ta shiga tana kallan Mama dake zaune tana waya sanyeda doguwar rigar kuwait me kauri sosai da hula tana waya da Baba Alhassan dayaje Umrah sbd bayajin dadi sosai manyanci yafara masa yawa sosai. Cikin sakewa dake hade da girmamawa tace "Mama ina kwana? Barka da tashi. Gyada kai maman tayi tana cigaba da waya da hannu ta nuna mata tarkacen kayan Falaq data bar mata a dakin hadda Ipad dinta da tana tashi bata ganta ba zata iya daga musu hankali azo ana bata lokaci gurin lallabata kafin fitarta. Tattara kayan Fiddausi ta fara tana dariya da cewa "Mama mutuniyarki ce kike cewa a tattara miki kayanta abar dakinki dasu, Tanajin haka zata fara ihun ta bata dake daman tace Daddynta kadai ne mutum a gidan nan" Qarasawa tai tana dariya Mama ma wayar ta gama ta kashe tana ajewa tace "Daman wannan me jajayen kunnuwan kowama a gurinta ba mutum bane Ubanta ne kadai mutum mu da sauran mutane duk witches ne" Dariya Fiddausi tasaki tana qarasa tattara dakin dayake fes tace "Ke mama tace tinda ke ne kika haifar mata daddynta baki qarasa zama witch dinba mune dai witches din da duk macen datake kallan mata daddy tace witch ce itama" "Dukan bakinta na dena shiyasa take fadar hakan da kuma shi uban nata dayake biye mata, A haka takeson ya qare rayuwar ba aure girma sosai yana zuwar masa sbd kawai 'yarsa tace batason kowace mace ta rabesa, Shima wannan qaton dayan uban nata ya zama wani tuzurun me zaman kansa ba auren tinda uban gidansa baiyiba duk sun qare a yawon duniya da aiki ba mata a rayuwarsu, Ni duk kin tado mun takaicinsu ma yanzu ana maganar Aljanar 'yarsa ta fara ihu tana kukan babanta bazaiso kowace maceba bataso shikuma yazo yana biyeta su siqani da safen nan abincin arziki ma nazo na gagara ci, Maza ficemun da kayanta a daki dan karma tazo nemansu ta hanani zaman lafiyar yau" Humidifier Fiddausi ta kunna tareda daukan kayan Falaq din ta nufi kofa tana dariya da cewa "Mama keda Aminiyar taki kike cewa ayi waje da kayanta" "Wannan batai Halin Aminiyar tawa me sunanta ba da 'yata Me sunan nata, Kina ganin 'ya a sangarce sai kukan banza da girmanta, Wata ran fasa bakin zanyi kowama ya huta sedai ubanta ya gashi da matse fuska ya hakura ba ruwana" Dariya Fiddausi takeyi tana ficewa dakin tareda sake duba agogonta taga time yayi kai tsaye ta nufi hanyar dakin Falaq din dayake hanya daya sa Palon Daddynta da bedroom dinsa. Tana isa hannu takai ahankali ta bude dakin tareda shiga kai tsaye tana rufo dakin tana isa bedside din lafiyayyan gadonta dayake cikeda pillows kusan guda 9 masu tsananin laushi da duvet dinda laushinda da kaurinsa ya cike gadon. Hannu Fiddausi ta miqa ahankali ta kunna wutar dakin dake gefen gadonta tana kallan Kyakkyawan fuskan falaq din da batabar komai na Mahaifiyarta ba da kuma wasu kamannin Sir AZIZ LIMBA dinba. Zaunawa tayi bakin gadon ahankali tana shafa fuskanta cikik kulawa da kaunar da itama take mai tsanani tana murmushi me kyau tana cewa "Falaq, Falaq baby, Alhmdulillahil lazi ahyana baada amatana wa ilayhir nushr, Good morning Bestien Daddynta, Time to wakeup" Bude idanuwansa tayi ahankali tana motsawa tareda maimaita adduar tashi daga baccin da Fiddausi ta gama karanta wanda ta sabane tin tana baby sun saba duk wanda ta tashi bacci gurinsa saiya mata dan haka ta saba duk zata tada bacci saita mata ita wani lokacin tareda adzkhar na tsari sbd Daddynta daya saba karanta mata shi a duk safiyar duniya koda baya nan tana farkawa shine yake fara kiran waya ya karanta mata tin tana baby haryanzu data fara girma. Tashi zaune Falaq tayi tana kallan Fiddausi cikin sake yar Kyakkyawar fuskanta da murmushi tace "Anty Fiddausi kinsan meyasa na tashi da smiling face? Wuyanta Fiddausin take shafawa ganin shatin wuyar rigarta daya kwanta mata tana murmushi itama tace "No Ms Falaq Aziz saikin fada witch dinki na sauronki" Wani Murmushin ta sake saukewa har tana dariya tace "Best daddy nai mafarki zai daukeni mi tafiyarmu mubar OldLady din gidan nan ta dena mun fada ta denawa BestDaddy fadan kawo mun Mummyn danace banaso" Dariya tayi tana Cewa "To amma hardani zaa tafi ko?? Sbd BestD din naki kinsan da bestMan dinsa zai tafi sbd babu inda yake tafiya batareda dashi ba dan haka kema da bestWitch dinki zaki tafi ko?? Kallanta tayi alamar shawara kafin tace "No,ke da Oldlady halinku daya kinason Daddynah yayi aure kema ai na taba jin kin fada a gaban Maman kuma kinfi bin bayan Maman....... Cikin komawa kaman qaramar babyn itama Fiddausi tace "Wat,inji waye yace inason Daddyn falaq Aziz yayi aure? Idanma na fada to inaga bana hankalina tinda kince dukanmu witch na possessing namu amma nikam banason kowace mace ta shiga zuciyar BestDaddy sbd zuciyarsa ta babynsa ne kadai ba gurin kowa, Babu wanda zataxo ta bata mana space" Qarasa zancen tayi tana danne dariyarta tareda nuna da gaske take. Kallanta falaq tayi tana karantarta kamar wata babba tana cewa "Should i trust you Fi?? 100 percent ma kuwa" Fiddausi ta fada tana bata hannunta cikin dariya. Qin bata hannunta tayi tana miqewa tace "Saina tambayi BestDaddy ko zan sake yadda dake coz oldLady tayi brainwashed naki i dont trust you both" Toilet take kokarin nufa da gudu Fiddausi ta riqota tana miqewa tsaye ta durqusa tana zare mata socks din baccin dayake kafarta me laushi kafin ta saketa ta nufi toilet dan brush ita kuma gyara dakin tafara wanda fadan luxuries dake cikinsa ma bata time ne. Koda Falaq ta fito Fiddausi ta gama gyara dakin tsaf ta kunna ac sbd Daddyn tin tana baby ya saka dokar baa kwana daki da ita har safe da ac Zata kwanta dashi qasa sosai kuma asuba nayi ake kashewa a tada ita sallah batareda duban qananun shekaruntaba sbd ta saba da sallan asuban akan lokaci tin tana rigima sosai idan an tadata da asuba harta fara sabawa sbd duk qarancinta to duk abinda Daddy dinta yakeso tana kokarin yinsa koda bataso da kuma duk yanda ya lalatata da gata sbd ba qaramin tsananin so takewa Daddyntaba. Tsananin son datakewa Daddynta ya saka sam batason kowace mace na sonsa ko ayi maganar yayi aure sam batason kowa ya rabi Daddyn sai ita kadai, Duk da akwai kuruciya sosai a lamarin nata amma da gaske har ranta batason daddynta yaso kowa sbd ganin takeyi idan yaso wani zai dena sonta ko ya rage ita kuma batako kaunar kwatanta Daddyn ya hada sonta da kowa ta kuma saka hakan sosai a ranta wanda ya fahimci da gaske take sai yaji baida raayin aure ko kadan a kusa barema baida time na mace bare Soyayyar duk da yana samun tayin aure daga manyan mutane ga yayansu amma baya buqata kuma baya boyewa yake dakatarwa sbd shi dan kai tsaye. A harkan business dinsa baida tausayi ko emotions ko kadan business kawai hakama tamkar wani mugun maye yake a duk abinda ya saka hannu sai wata irin nasara me girma taxo shiyasa manyan da suka kaine yanzu kawai abokan businesses dinsa shi kansa manyan da suka amsa sunane kadai ke hulda dashi sbd nasararsa binsa take koina ya saka hannunda kafa hakan ya saka yayi wata irin suna da shaharar da sunansa yake yawo a tsakanin manya da duniyar masu abin duniya kawai. Lucky Billionaire Monster ake kiransa a cikin Business tycoons da suke hulda dashi gashi da wani irin farin jini da kwarjinin dayake sakasa samun respect fiyeda shekarunsa a gurin manyanma hakama kudinsa ya saka respect dinsa yake ninkuwa gashi da kamewan datake saka manyanma da yawa shakkarsa. Bayan businesses dayake da companies dayake dasu qasashe da Nigeria a harkan Business na motocin Business dinsu da Alh Saad wanda shima ya gama miqawa yayi nisa sosai a daula da samun power Shine yake ranking No 2 a business na motoci kaf dan haka gaba daya ma yake wahalar gani. Zaunawa sukai da Fiddausi a gaban mirror tana tayata shiryawa kafin ta nufi closet dinta tana dauko mata kayan da zata saka tana sake mata dadin bakin itama batason BestDaddy yayi aure. #MAMUH #AZIZ AY LIMBA #FALAQ AZIZ #JANNAH ZAD #REVENGE #SAYD ZAFAFA BIYAR KALBIM 500 mamuhgee A DUNIYATA 500 Huguma AJIYA A DUHU 500 Billyn Abdul KIRJIN ME HANKALI 500 Miss xoxo Pay at 0022419171 AccessBank Maryam sani gummi Shedan biya 09033181070 Or mtn vtu at 09032345899*_Arewabooks@Mamuhgee_* 32 *ZUZEAM VENTURES* Best APHRODISIAC 08144015291 Aslm barkanmu da wannan lokaci Ina Mai farin cikin sanar daku cewa Zuzeam ventures takawo maku ingantattun magunguna masu inganci cikin Aminci Muna da kaya kamar haka Mallaka Maganin sanyi Maganin cire tumbiMaganin farin jini Maganin matsiMaganin mata Maganin sa ni’ima da dandano Dulka Amare Set na gyran jiki Set na amarya Tabaje tsumin Gomba Xuma kiba ta hips and Brest Magungunan gyran Brest Magungunan Karin hips Maganin sliming Muna da kaya masu inganci  cikin sauki da rahusa Ina wadda keneman mallaka sahihiya quaranty wlh hajiya kixo ga zuzeam ventures xakiji ddin mallaka duk fadin ran ogah duk fadansa wlh sai yyi sanyi 08144015291 Idan maganin mata kikeso akwai Idan gyran jiki kikeso gyran fata gyran Brest magungunan sa kiba da hips DOMIN samunta Kai tsaye kira wannan no 08144015291 DOMIN mgn da ita whatapp 08144015291muna tura kayanmu ko ina cikin iKon allah 🥰👌🏻 Bononza Bononza Tsimin mangoro 1k🥭 Tsimin dabino 1k Gumba ukku balai 700 Gumba aya da nonon rakumi 700 Garin kafi ciccibi 500 Garin bata gaban kishiya 500 Matsin mallaka tada zaune tsaye 2500 Turaren mallaka ba aba mai kishiya 2500 Total kayan 9500 Za a bakisu akan 3800 Kuma mutun goman farko nadakyautar Abun 2k 🗣️🗣️🗣️🗣️🗣️🗣️ ASSALAMU ALAIKUM ALHAMDULILLAH YAN UWA  NEW PROMO YA KAMMALA💃🏽💃🏽💃🏽😁😁😁 da 5k dinki ki kwashi kayan 12k hajiyata 💃🏽💃🏽💃🏽😃🙃Kazar gadali ta mallara Rabi 3500 Tsimin gam gam 1500 Ruwan kara zunzurutun dadı😋800 Garin 7in1 1k Gumba 3 balai 500 Gumba kwakwa da dabino 500 Infection ruwan tsarki 1k Garin zunzurutun dadi 1200 Matsin ba a fira d wando 500 Matsin infection mai matse mace gam 500 12k All at 5k kedai dannan link dinnan don samun naki ki maza kiyi bucking koda kudinki saida Rabonki ******* Sauraronta Falaq kawai keyi tana cewa "Sai nayi shawara da BestDaddy zan san should I trust you or not" Fiddausi dariya takeyi tana cigaba da tayata hada kayan zuwa camping din dazasu na school na yara tana cewa "Na bar team din Mama na dawo team Falaq... Katseta falaq din tai da cewa "Falaq Aziz" Sorry na falaq Aziz na manta princess din gidan batason ana raba sunanta dana Daddynta" Straight jean daya lafe jikinta da white Cardigan me kauri da tsayin datazo har cinyarta ne Fiddausi ta tayata sakawa sai kuma jacket itama me kauri da qaramar veilhijab da iyakacinta wuya da sai socks data saka ta duba time ta zare jacket din tabar Cardigan kafin a tashi fitan, Qamshin turarenta me sanyi ne na yara irin shekarunta yake tashi a jikinta da dakin, ta nufi kofa tana ficewa zuwa gurin daddynta sbd tana tsananin farin cikin ta wayi gari ace daddynta na gari zata gansa a safe kafin komai. Tana fitowa palonsa take kokarin nufa Kofar palon Mama ta bude maman na fitowa tana kokarin saka kiran numbern data kasa nemowa da kanta tana kiran Fiddausi tazo ta nemo mata. Cikin ihun daya saka maman firgita tana saurin ja da baya wayar hannunta na faduwa falaq ta saki tana rufe idanuwanta da sauri tana cewa "No no no,bazan fara saka Mama a idonaba, Ina fara ganinta shikenan idona zai zama wani iri ayau, Idona babu wanda zai fara gani se the No 1 handsome and the most beautiful and amazing BestDaddy in Falaqs Universe..So i can't let my beautiful eyes su fara da ganin oldLady. Fiddausi datake bayanta maman ta kalla tana danne dariyarta Mama kuwa data saba da wannan iya shegen na Falaq din hade fuska tayi sosai tana gyara tsayuwarta daga firgitan datai tana cewa "Fiddausi dakyau, Kina kallan yarinyar nan ta zuba wannan ihun tana kusa dake baza kiwa bakinta mugun dukan da saiya fashe ba kika tsaya a bayanta kina dariya tana cewa Uwar ubanta mayya ko?? Falaq na jin hakan ta saka hannuwanta tana rufe kunnuwanta tana bin bango idonta a rufe tana cewa "Har muryan kowa bazanji ba Muryan datafi na kowa dadi and Nutsuwa" Nufota mama ke kokarin yi tana cewa "Kamo mun ita Fiddausi ki ban nan... Tana jin hakan da gudu ta qarasa hanyar palonsa tana Kiran sunansa da karfi sbd tasan Fiddausi na kaita Dukanta Maman zatai sbd a duniya ita kadaice take dukanta ko zaneta Daddynta baya ko dago kai bare iya cewa komai amma ko school baa dukar masa 'ya sam bai nuna zai yadda ba dan haka kaf rayuwanta maman kadai take tsoro duk da hakan baya hanata fadan magana sedai maman ta bige bakin amma bayan mama sbd Daddynta daya tsaya mata bata tsoron kowa duk da tana qarama amma sam batajin tsoron kowa a ranta sbd ubanta ya tsaya mata. Ihun kiran Daddynta datake ya isa har makeken dakin Sayd dayake bacci cikin lafiyayyan gadonsa sanye da kayan baccin Logous Ash cikin duvet dinsa me laushi dayake tashin qamshin jikinsa da gama kama turarensa.. Sama sama yake jiyo ihun nata yana shiga kunnensa dan haka motsawa yayi Ahankali tareda miqa hannunsa daya batareda ya bude idanuwansa ba ya janyo wani pillow dayake gefensa ya rufe kunnuwansa yana komawa baccinsa. Mama cewa tai "Fiddausi idan baki kamo mun ita kika kawo mun ba zaki fuskanci bacin raina kuwa ayau" Falaq na jin hakan ta qarawa kafafunta gudu tana isa kofar palon ta miqa hannu zata bude aka bude kofar palon.. Wani irin nutsatsiyar qamshi mai sanyin dadi dayake tabbatarda tsadarsa a shaqa daya sanyin ac ya kado waje daga cikin palon wanda har inda mama take tsaye yakai yana sauya numfashin main babban palon gaba daya.. Bude kyawawan idanuwanta da suke sak nasa falaq tai tana kallo tin daga fararen yatsun kafarsa dasuke wani irin fes kaman baya fita dasu sanye cikin versace slippers, Sanye yake da black pyjamas Basu tsantsi sai jacket me girma daya sako dazai fito daga bedroom dinsa sbd tashinsa kenan daga bacci muryanta ta fiddosa. Fuskansa datake wani irin fresh ta kalla ko morning face dinsa ganin takeyi tafi duka daddies din duniya kyau dan har fada takeyi a school da fahari Daddynta is the most handsome mutum dayafi kowa kyau. Hannuwansa dake cikin aljihun jacket din jikinsa ya zare yana bude hannuwansa kafin ma ya karasa kai hannuwan nasa akan fuskanta ta fada jikinsa tana cewa "Yesss BestDaddy idanuwan Falaq Aziz suka fara gani ba Oldy ba" Da farin ciki sosai a muryanta da yanayinta ta qarasa zancen tana qanqamesa cikeda tsananin son mahaifin nata. Wani Kyakkyawan murmushin daya saka Fiddausi saurin sauke kanta sbd yanda ta kusan dauke wuta agurin ya sake mai sauti yana durqusawa ya ajiye gwiwowinsa qasa sbd ta rungumesa da kyau ya rungumeta shima yana gyara mata veilhijab dinta ya bude baki da muryansa dake cike da wani irin nutsuwa da steez daya gama kamasa yace "Bazaki dena tsokanar Mama ba ko? Kinason ta dokamun bakin my one and only Falaq Aziz" Sakinsa tayi tana juyawa ta kalli Hanyar da maman take tana riqe hannunsa cikin nata tace "To ni kasan ai bazan yadda na fara ganinta ba banfara ganin My Besty ba" Hancinta ya shafa yana kallan Fuskan Ummitansa akan tata ya sake sakin murmushin daya fito daga asalin zuciyarsa yanajin kaunarta data uwarta da bata duniya suna yiwa zuciyarsa yawan da yakejin ko tinanin komai bazaiyiba akan basu ransa, Idan yana kallan fuskan falaq duniyarsa nutsuwa take tana samun sanyi da nitsatsen farin ciki me yawan gaske duk da rayuwarsa na cikin wani irin bushewan da har abada bazata sake jiquwa ba sbd rashin Ummitah wadda rashinta shine asalin ciwonsa da ba warkewa bawai na rashin iyayensu ba. "Amma falaq Aziz tasan cewa Maman itace maman Bestyn nata fa,kuma shi Bestyn Ai yana son mamansa sosai... Bata fuska tayi tana cewa "Ai sbd itace ta maman Bestyna ya saka nake tsoronta,kuma idan baka nan ai ina jin duk abinda ta fada, Nidai Daddy karka bari ta dukarmun baki, Duk ta qara masa tsowo sbd duka gashi yanadon ya dena kama da naka" Mama data nufosu taji abinda take fada cikin quluwa tace "AZIZ kana jin abinda take fada sai murmushi kake mata ko? Dagowa yayi yana kallan Maman da sauran murmushin akan fuskansa dake cikeda da kwarjini ya kalli maman yana cewa "Mama barka da safiya" Amsawa tayi tana kallan Falaq din data boye bayansa tana cewa "Arzikinki daya yau tafiya zakiyi da sai kin kwana biyu bakinki baiyi magana ba a gidan nan" Turo baki tai tana qin cewa komai sbd maman na cewa Daddynta ya matsa gefe matsawar zaiyi dan haka tai shiru tana turo baki. Shi kuwa murmushi kawai yayi sbd mamance kadai take discipline na Falaq din sai Sayyid da shima yake dan bude mata ido amma idan baa gaban Babanta bane. Maman magana zatai dashi dan haka Falaq din ta shige palonsa shi kuma suka koma palo da maman sukai maganar rashin lafiyar Baba alhassan tukuna ya koma dan shiryawa sbd lokacin fitowansa ma baiyiba rigimar falaq dince ta fiddosa. Yana shiga palon tana zaune tana duba abu a ipad dinta tana dariya sosai, Kai tsaye Bedroom dinsa ya nufa ya rufo Kayan jikinsa ya zare lafiyayyar fatarsa ta bayyana tana daukan ido sbd samun hutu da tsadaddiyar gyara da original skin products masu tsada da kyau. Toilet dinsa dayake da girka sosai ya shiga tareda nufar shower ya sakarwa kansa ruwan dumi yana rufe idanuwansa ruwan na sauka akan fuskansa suna ganganrawa jikinsa suna dumama jikinsa. Bai wani jima sosai ba yana wanka dasu gyaran fuska da sauransu kafin ya fito daure da babban towel me kauri brown jikinsa na fidda qamshin shower Soap dinsa na Ocean seaweed. Goge jikinsa yayi a natse sa wani clean towel din kafin ya fara shafe jikinsa da bodymilk da mix na oils na Ngenas da suke saka jikinsa glowing da kyan gani da wani irin soft ya shafa perfs dasu bodyMist da sauransu kafin ya gyara fuskansa yai brushing gashin kansa dayake a kwance da santsi irin na asalin filani. Bai dauki mintina sosaiba bayan gamawa ya shiya cikin Navyblue jeans da White long-sleeved shirt data nutsu a jikinsa sbd tasan kudin daya siyeta. A cikin tarin tsadaddun designer agogayensa dake jere a doguwar glass drawer daya ya bude ya dauko black cartier ya saka sai navy blue Lv fcap daya sako ya fito yana daukan wayarsa ipad dinsa datake iri daya sak da 'yarsa. Yana fitowa koina a palon an sake gyarasa kamshi da sanyin ac komai neat dukda bawai datti ko wani hayaniya a palon komai unique,simple and luxuries ne kawai. Fiddausi ce take gyara komai na bangarensa dana Falaq saina Sayd da mama amma sauran gidan masu aiki ne ke aikin. Tana ganin fitowan Daddyn nata ta ajiye abinda yake hannunta ta miqe tayo gurinsa tana cewa "You're morethan handsome MyBesty" Juyowa yayi kalleta tana hada hannunta da nasa ta riqe yace "And you?? Dariya tayi tana dawowa gabansa tana tafiya da baya suna tafiyar a haka tace "I'm my father's daughter,so I'm the beauty itself" Murmushi me nutsuwa kawai ya sake mata suna fitowa palon inda suka tarar da Mama na zaune tana magana da Fiddausi dake fada mata yanda sukai da Falaq da safen tana dariya. Sayd kuwa a tsaye yake shigowansa kenan palon yana waya ganinsa ya sakasa qarawa ya karbi ipad din datake hannunsa yana masa barka da fitowa ya koma gefe yana cigaba da waya akan baqin da zasu tattauna dasu gashi AZIZ din yau ranar 'yarsa ce sbd da kansa zai rakata sbd kowa iyayensa zasu tafi dan haka shima yace a dakatar da duka schedules nasa na kwana biyu sai Falaq Aziz ta sun gama camping dinsu. Hakan yasak yaketa kokarin ji da ayyukan da baqinsu tareda clearing schedules din yaji da komai. Dining suka nufa dukkaninsu Falaq na sake boyewa gefensa tana leqa mama da ko kallanta bataiba tace masa "Daddy zan bata da Anty Fiddausi tana fadawa mama sirrina" Kallanta yayi yana cewa "Oh no indai hakan ne taci Amanar Falaq Aziz" "Yes Daddy,Kuma tace tana bayana amma tana maganar sirrina da mama i heard them not once" Mama data juyo tana harararta ta kalla tana qara shige masa tace "Did you just see that Daddy? Jira take kayi tafiya zata dakeni for sure akan na fada gaskia" "No Falaq bakinki ne is to talkative shiyas Mama ke dukansa so ki dena kiga bazata dakeki ba" #MAMUH ZAFAFA BIYAR KALBIM 500 mamuhgee A DUNIYATA 500 Huguma AJIYA A DUHU 500 Billyn Abdul KIRJIN ME HANKALI 500 Miss xoxo Pay at 0022419171 AccessBank Maryam sani gummi Shedan biya 09033181070 Or mtn vtu at 09032345899*_Arewabooks@Mamuhgee_* 33 *KALPANAH COLLECTION* 08105064494 Shin ke daliba ce ko kuma uwa wadda har yanzu bata daina rokon urgent 2k a wurin yan uwa da kawaye ba,tou nesa tazo kusa domin kuwa na kawo miki maganin matsalarki,domin kuwa *Kalphanah Collection* ta shirya tsaf domin taimaka wa duk wani dan kasuwa ko kuma wanda yake son fara kasuwanci.A *Kalphanah Collection* muna saida kaya kama daga Jaka,Takalmi,Atamfa,Laces,Kayan yara da kuma kayan kitchen.Wani abun mamakin ma muna saida kayan mu ga masu siyen daya ko kuma sari,ga waenda basuda jari ma mun tanadar masu hanyoyi daban daban da zasu fara neman na kansu.Hajiya kina gida kwace zaki dinga  jin saukar kudi a asusun bankin ki.Ga musu fuskantar qalubale a kasuwancin su kuma an kawo muku sauqi domin kuwa an bude muku group dinku da zaku dinga tattauna matsalolin ku. https://chat.whatsapp.com/JMSe2The4Q2F5tLdzGduyC Kedai idan kin shirya ki dannan link din nan na kasa domin shiga group dinmu ki ganewa idonki kunsan ance gani ya kore JI Karki yadda ki wuce bakiyi joining group din nan ba domin kuwa yanzu sallah tana qaratowa ko bakiyi kasuwanci ba zaki siya domin amfanin ki na yau da kullun kuma ko baku buqata yanzu nan gaba zaku iya neman ta. Siyen na gari maida kudi gida. 08105064494 ************ Shiru tayi tana lafewa gefensa har suka isa dining room din suka zauna Fiddausi cikeda girmamawa tai masa ina kwana da barka da fitowa tafara serving nasu daidai nan Sayd ya shigo yana ajiye wayarsa da ipad din hannunsa kan Console mirror dayake room din yazo ya zauna yana yiwa AZIZ din barka da safia cikeda girmamawa kafin ya kalli falaq datai sanyi a kujeran gefen daddynta sbd ya mata fada kaman bazata bude baki tai magana ba sai ta tina Daddynta sam baya barinta yiwa Sayd ba daidaiba ko kadan dan hakan ne ma take ganin Sayd din kamar kishiyarta a gurin daddynta wasu lokutan sbd Sayd koyaushe koina yana tareda daddynta yafita kusanci da daddynta gashi dan haka ta bude baki tana kallansa kaman zatai masa kuka sbd shagwaba tace "Goodmorning Uncle" (shi ya zabi ta kirasa da hakan) Dariya yai mata yana amsawa sbd yasan jira take yace me akai mata tafara kukan banza da baya mata wuya duk data fara girka amma sam baya jin wuyar kuka ko kadan. "Falaq din Mama yaya dai?? Kallansa tayi da sauri bayan ta kalli maman da sauri wadda bata kalleta ba ta dawo da kallanta kan Uncle din qasa qasa batason Daddynta yaji sbd baa hayaniya idan zaaci abinci yana gurin hakama batason maman taji tace "Falaq Aziz ba mama nidai" Maman taji ta hakama daddyn dan haka ya dan dago fararen idanuwansa ya kalleta tayi shiru tana kallan Sayd wanda yake mata dariya ahankali dan yasan abinda zata fada daman dan ta tsani a kira sunanta batare dana ubanta ba. Abinci suka fara ci batareda kowa ya sake magana ba cikin nutsuwa, Kallan Daddynta takeyi yanacin abincin a natse, Kallanta yayi jin idanuwanta akansa, Tissue ya miqa hannu a natse ya dauka ya goge mata gefen bakinta ahankali kafin ya kalli abinda yake kan plate nata ya maida idanuwansa akan fuskanta yana cewa "Bakyaso ne?? Girgiza kai tayi tana sake murmushi me kyau tace "I love you besty" Murmushi me sanyi ya sake mata yana cigaba da cin abincinsa Itama cigaba tayi da cin abincin tana cika da farin ciki sbd duk duniya babu abinda takeso sama da Daddynta, Kaunarsa take sosai da gaske shiyasa bata gajiya da kallansa tana jin idan mamanta tana tare itama saita ringa kishinta akan Daddynta. Suna gamawa shine ya fara daukan Tissue ya goge bakins bayan ya sha ruwan dumi kadan dan bai cika sakawa cikinsa abu me sanyi sosaiba. Miqewa yayi Sayd ya miqe shima yana bin bayansa tareda daukan wayarsa dake vibrating kira na shigowa ya dauka yana dakatawa ya juya ya nufi office din AZIZ na gida yana amsa wayar a natse harya isa ya kashe yana bude ipad dinsa yafara duba sakon dazai bawa AY din. Shigar office din ya nufi laptop dinsa dake aje ya kunna dan duba sako da aka turo. Yana duba sakon karance bayanin yayi tareda duba dukkanin bayanan da aka tiro tareda shi kafin ya kashe ya rufe ya fito ya nufi palon AZIZ din wanda yake zaune a natse yana waya wadda ta sakasa tsayawa jiran ya kammala. Ya dan jima yana wayar kafin ya gama ya ajiye wayar yana kallan Sayd wanda ya matso ya miqa masa ipad din hannunsa yana cewa "Duka anyi draftin komai na Fris And Co hakama anyi rescheduling haduwansu Vilias da Zuwansu. Sakon email dayake kan screen din ipad din yake karantawa yana sauraron Sayd din wanda komai yake cikinsa yana sake masa bayanin a natse da girmamawa. Ajiye iPad din gefensa yayi bayan ya gama duba komai yace "Meye feedback na tafiyan Falaq?? "An duba komai babu matsalar komai kaman yanda ta fada 3days ne and anyi arranging komai so all is good sai... Wayarsa suka kalla su dukan sbd kiran daya shigo ya katsesa. Ganin me kiran ya saka AZIZ cigaba da jiran bayanin Sayd din wanda ya kallesa da girmamawa yana budo sakon wanda shine kusan karo na hudu suna turo buqatar son ganin AZIZ LIMBA din amma sam ba damar hakan. Cikin nutsuwa Sayd yace "Saleem Zadeen ne yake sake turo buqatan son ganinka tareda Fiars" Shiru yayi batareda bawa zancen mahimmanci ba yace "Reject them" Kallansa Sayd yayi kafin yace "Yes" yana rejecting nasu kai tsaye ba tsayawa ya juya ya fice bayan ya sanar dashi nan da mintina goma zaa tafi mota is ready. Acan Palon mama kuwa tsare falaq tayi tana mata fadan surutu da iyayinta akan tafiyar da zasuyi wanda bata taba kwana ba gida ba sai wannan karan. Gyada kai Falaq din keyi kamar tana jin fadan da ake matan tana gudun tace aa maman tayo kanta dan haka tai tuba da nutsuwar dole har aka gama tukuna maman ta janyota tana gyara mata zaman jacket din da Fiddausi ta kawo mata t saka tareda jakarta da qaramar akwatinta na lv me tsadan gaske suka fito maman na mata adduar tsari da lallabata kaman ba tin safen suke fada ba. Koda ya fito sanyeda Farin goggles dinsa sallama kawai yayiwa maman falaq ta kama hannunsa suka fice tana murna. Sayd daya gama sakawa an saka kayansu a mota bude masa motar yayi yana kallan Falaq dake murna tana kallansa tana masa magana da hannu alaman tana farin cikin tafiya da daddynta. Motar suka shiga shima ya zagaya ya shiga gaban motar sbd ba shine zaija ba driver ne. Suna fara tafiya ta dawo gurinsa tana kunna masa children's show din datake kalla tana dariya shi kuwa zubawa hannayenta idanuwansa yayi shiru batareda yace komaiba wanda hakan ya saka motar shiru sai ita kadaice take shaaninta. Tafiya me tsawo sukai har zuwa inda zaayi, Parking sukai yana kallan gurin wanda kusan iyayen yara da yaran sun riga sun fara camping dan haka suma qarasa sukai gurin Manyan teachers din nata sukai reporting cikin girmmawa malaman suka gaidasa suna masa barka da zuwa tareda dan yiwa falaq wasa. Koda suka juyo Sayd da kansa ya fara buga musu tasu runfar dan haka zagayawa falaq din ta kama hannunsa sunayi a gurin tana murna sbd sam baya barinta shiga yara ko kadan bayan school koyaushe tana killace a gida dan haka takejin dadin wannan lokacin sosai daya barta kuma haryaxo da ita. Suna cikin zagayawa wayarsa tayi ringing ya dauki wayar a natse yana komawa nesa da mutane sosai dan amsawa ita kuma ta nufi inda ake siyan kyautukan da iyaye zasu siya su bawa yaya da wanda yayan zasu siya su bawa iyayen duk yana cikin wasa da abubuwan da zaayi musu dan haka tana isa farin cikinta ya qaru sbd har taga abinda zata bawa daddynta. Da gudu ta koma gurin Sayd tace yazo ya gano. Janyosa tayi da sauri tana cewa ya siya mata kafin wani ya siya. Suna isowa gurin da gudu ta nufi farar shirt da aka rubutawa "MY BEST MAN" tace "Uncle ka biya da sauri ina so" Kallan shirt din yayi hade da fcap dinta zaiyi magana tace "Please kafin wani ya biya inaso zan siyawa Besty" "Ok ok naji bara na biya to" Kokarin ciro wallet dinsa dake cikin wandonsa yayi Suka tsinci daddadiyan muryanta mai cikeda farin ciki da nutsuwa itama tana cewa "Hey miss ina buqatan wannan shirt din" Juyowa da sauri falaq tayi tana saukar da idanuwanta akan. Jannah da batasan da falaq din a gurin ba hannu ta miqa zata ciro rigar Falaq tayi saurin cewa "Excuse me miss,Wannan nawa ne muna kan biya" Juyowa Jannah tayi ahankali cikin nutsuwa ta dora idanuwanta akan Falaq datai maganar da nuna tsananin sonta da rigar. Fuskanta ta zubawa fararen idanuwanta tai mata kallan seconds. Batareda tace komai kyan yarinyar da wani kwarjinta daya cike mata ido ya sakata sake wani Kyakkyawan murmushin daya sake bayyanar da kyanta itama daya saka falaq din Zuba mata ido a ranta tana cewa she's beautiful amma bazan bar mata rigan da zan bawa daddyna ba. Cikin murmushin dayake qarawa Jannan burgewa ta bude baki tace "Hey beauty, Kibarmin pls i have someone very very very special da zan bawa as a tsaraba am going back home pls pls pls Baby" Baya falaq taja kadan tana kallanta kaman wadda tai sa6o tace "Very dinki uku ne ni kuma nawa da zan bawa is very very very very very very very special, Ni yama fi naki komaiba.... Dariya maganar ta bawa Jannah ta sake kallanta da mamaki me tsananin gaske tace "Tace pls Beauty kiban zan ninka muku kudin so biyar am giving it to the love of my life... Katseta falaq tayi da cewa "No my BestDaddy shine ya dace da wannan rigar sbd kalman shine tafi dacewa dashi akan kowa" Fara jin haushi jannah tayi ta kalleta tace "Ba da tsofi rigan ta dace ba so pls stop wasting my time ki bani rigan kafin kwace a hannunki wanda zaiyi payment dinma gashinan kina gani ya tsaya magana da wani" Batareda falaq ta juya kallan Uncle dinta ba tace "Did you just call my daddy tsoho? Daddyna shine yafi duk mazan dake koina kyau da komaima ko kyansa ma ke bakiyiba ai" Murmushin takaici jannah ta sake tana kallan bakin falaq din dayake rashin kunya ba tsoro amma sbd takaicin maganar tata wayarta ta ciro tana miqawa gaban fuskan falaq tana cewa "Kin taba ganin me kyau da class din wannan a qaraman rayuwarki?? Kallan hoton kan wayar falaq tayi wanda Kyakkyawan fuskan Ammar zad take bayyane yana zaune sanyeda suit farare yayi kyau sosai da murmushi akan fuskansa. Kallansa ta sake yi kafin ta dago ta kalli jannah din ta sake mata wata dariyar data saka jannah din itama dariyarta sbd ta dauka dariyar ta sakar mata ne. Dariya sukai sosai kafin falaq ta dena dariyar ta kama hannunta zuwa gurin Daddynta dayake nesa dasu sosai yana waya har lokacin. Kwace hannunta jannah tayi sbd sauri takeyi ita bata time din batawa daman biyowa tayi ganin wata a gurin. Cikin sakewa Falaq tace "Kin nunamun naki zan nuna miki nawa" Kin tafia jannah tayi dan haka sbd tai mata wayo taje ta karba rigar sai tace "Kije kizo dashi gani nan ina jira ina kallanki kada tsoron ganin Best Man ya sakaki guduwa dan bazaki iya nuna daddy dayake tsoho ba" Matse fuska falaq tayi tana cewa "Bestyna baya zuwa kiran kowa saina Falaq Aziz and bazan kirasa sbd kowa ba sai sbd kaina dan haka bazan kirasa nan ba amma wait and see... Nufarsa tayi da gudu tana kusan kaiwa gurinsa ta kira sunansa ya juyo a natse gaba dayansa yana kallan yanda take tahowa da gudu. Jannah dataso falaq din na tafiya ta juya ta karbi rigar ta tafiyarta Juyowansa ya sakata tsayawa a gurin tana kallan fuskansa dayake kallan Falaq da dukkanin kulawansa batareda ya kashe wayar dayake ba. #MAMUH ZAFAFA BIYAR KALBIM 500 mamuhgee A DUNIYATA 500 Huguma AJIYA A DUHU 500 Billyn Abdul KIRJIN ME HANKALI 500 Miss xoxo Pay at 0022419171 AccessBank Maryam sani gummi Shedan biya 09033181070 Or mtn vtu at 09032345899*_Arewabooks@Mamuhgee_* 34 *KALPANAH COLLECTION* 08105064494 Shin ke daliba ce ko kuma uwa wadda har yanzu bata daina rokon urgent 2k a wurin yan uwa da kawaye ba,tou nesa tazo kusa domin kuwa na kawo miki maganin matsalarki,domin kuwa *Kalphanah Collection* ta shirya tsaf domin taimaka wa duk wani dan kasuwa ko kuma wanda yake son fara kasuwanci.A *Kalphanah Collection* muna saida kaya kama daga Jaka,Takalmi,Atamfa,Laces,Kayan yara da kuma kayan kitchen.Wani abun mamakin ma muna saida kayan mu ga masu siyen daya ko kuma sari,ga waenda basuda jari ma mun tanadar masu hanyoyi daban daban da zasu fara neman na kansu.Hajiya kina gida kwace zaki dinga jin saukar kudi a asusun bankin ki.Ga musu fuskantar qalubale a kasuwancin su kuma an kawo muku sauqi domin kuwa an bude muku group dinku da zaku dinga tattauna matsalolin ku. https://chat.whatsapp.com/JMSe2The4Q2F5tLdzGduyC Kedai idan kin shirya ki dannan link din nan na kasa domin shiga group dinmu ki ganewa idonki kunsan ance gani ya kore JI Karki yadda ki wuce bakiyi joining group din nan ba domin kuwa yanzu sallah tana qaratowa ko bakiyi kasuwanci ba zaki siya domin amfanin ki na yau da kullun kuma ko baku buqata yanzu nan gaba zaku iya neman ta. Siyen na gari maida kudi gida. 08105064494 ************ Falaq riqo hannunsa tayi cikin farin ciki da murmushi tana janyosa dan ya siya mata rigar da kansa. Tinda suka tinkarota taji numfashinta na fita da sauri bugun zuciyarta na qaruwa ahankali idanuwanta na kasa daukewa daga kansa, Aura dinsa ce gabaki daya ta cike ganinta harma da hanci da bugun zuciyarta dayake tsananta ahankali ahankali, Waya yake har lokacin a cikin nutsatsiyar turancin da muryansa datake fita ahankali a kame ba hayaniya cikin wani irin steez. Suna kawowa daf da ita qamshinsa me tsananin sanyi da nutsuwa da tsadar gaske na Tomford ya sauya iskan datake shaqa da gurin datake tsaye. Ta gefenta ya wuce batareda ma yasan da akwai rai a gurin tsayeba yana nufar inda Falaq ke jansa wadda itama suna wucewa juyowa tayi ta kalli Jannah din wadda take tsaye a gurin batareda ta motsa ba bare juyowa ta kallesu.. Sayd da already ya biya kudin suna isowa ya miqa mata jakar da aka saka kayan Ta karba tana murna batareda ta saki hannun daddynta ba suka bar gurin batareda ta juyo ta kalli jannah ba sbd batason ta sake kallan Daddynta sbd tanada kyau. Jannah kuwa daga inda take tsaye bata juyoba wucewart tayi ta nufi motarta datai parking ta bude ta shige tareda barin gurin tana dan dafe setin zuciyarta dayake bugawa da karfi ahankali tana dora idanuwanta akan titi kuru ta nufi gidan Daddy mahmoud datake zaune acan. Falaq kuwa daddynta ta bi yana waya har lokacin ya zauna kujeran hutawa da Sayd ya hada masa da rumfa tareda table da abubuwan falaq din suke kai sau ipad da roban ruwan dayasha ya rage akai. Wayarsa yaci gaba da yi a natse bayan ya zauna kenan. Farin goggles dinsa ya zare ajiye gabansa yana dago fararen idanuwansa ya zubawa falaq dake wasa sosai a gabansa tana tsalle tareda abokanta da teachers dinsu uku da suka shiga cikinsu suna sake karfafa tsallen da farin cikin wasan. Sayd dayake busy mutum ne dan kusan shine office din AZIZ da kansa kokuma yace shime computer dinsa dan hakanne ya saka shi baida wani hutu koyaushe aiki ne kawai da handling abubuwa. AY na gama wayar ajiyeta yayi tareda sakata do not disturb sbd bawa 'yarsa cikakkiyar time da nutsuwansa dan haka a hankali cikin nutsuwa ya dora kafarsa daya akan daya ya jinginar da bayansa a kujeran yayi relaxing yana folding hannuwansa a zuba mata ido yana kallan yanda take dariya. Dariya da farin cikin falaq shine yake sake bayyanarda tsananin kamarta da mahaifiyarta da kamannin dabiunsu shiyasa a irin wannan lokutan zuciyarsa take sanyi da tsananin kewan Ummitah wadda yake kan karban therapy har yanzu da lokaci me tsayi yaja na rashinta amma haryanxu zuciyarsa bata taba dawowa daidaiba sbd ya riga ya samu raunin da ba lallai ya warkesaba har yabar duniya sedai yana iya kokarin hana hakan kaisa qasa sedai da dama wasu lokutan saiya kusan kaiwa kasa kaman bazai iya daurewaba Sayd ne a tsayin dakan ganin hakan bata faru ba, Babu wanda yake gani ko ya taba sanin rauninsa sai Sayd wanda yasan zuciyarsa rasa jarumtarta takeyi idan ciwon rashin yar uwarsa ya taso masa wanda hakan ya riga yayiwa rayuwarsa illan da Allah ne kadai zai tallafesa. Itama kallansa takeyi akai akai tana nuna masa abinda suke cikeda farin cikin kasancewansa a gurin.. Lumshe mata fararen idanuwansa kawai yakeyi tareda gyada mata kai a natse yana murmushi a duk lokacinda ta nuna masa. Ahaka suka jima kafin lokacin sallah yayi ya miqe sayd ya kawo masa ruwan da yai alwala sukaje sukai sallah suka dawo a lokacin ta gaji sosai itama sallan tayi kafin tai lunch tareda kowa har lokacin yana nesa zaune cikin tint yana dan duba sakonni tareda sauraron Sayd wanda ZAADENs suka sake nema yai rejecting nasu kai tsaye sbd bayajin Har abada zasu samu abinda sukeso daga AZIZ LIMBA dan sune sukeson ganinsa kuma suke buqatan ya amsa gayyatarsu zuwa garesu wanda indai hakan ne to kome sukeso garesa bazasu taba samu ba har gwara su su kawo kansu da kansu to akwai yiyuwar su samun dan haka kwata kwata yama qi sake sanar masa request din nasu yake rejecting kai tsaye. Har dare sosai aketa party da wasanni tareda wasu abubuwan na ilamantarwa ga yara da wanda suka fara zama yan mata da matasa har kusan 9 tukuna aka gabatar da gurin baccin yara da tint masu kyau da kowa iyayensa suka tanadar masa dan haka ba bata lokaci Falaq da aka gama gyara mata komai kaman wadda tafi kowane 'da a gurin sbd Daddynta da uncle dinta babu abinda baa tanadar mata ba da zata buqata. Daga ita har Daddynta Sayd bai taba wasa da duk lamarin daya shafi buqatarsu ko kulawa ba musamman shi din sbd hakan ne ma yasa babu wanda yasansa duk duniya irin Sayd, Lafiyayyar tanti da a wadace da nutsuwa aka hada masa shida Falaq din dan haka ba damuwa ko wani rashin jin dadi tayi baccinta shi kuwa bai wani yi baccin ba. Sayd kuwa nasa tantin daban, Daurewa sukai washe gari aka qarasa sauran activities din aka sake kwan suka tattaro suka dawo cikin farin ta samu abinda takeso karan farko da daddynta yabarta ta shiga irin wannan activities din kuma ya tafi da itan dan haka koda suka dawo bayan gama gaisawa da mama bai tsaya komaiba ba ya shige bangarensa dan yana buqatan hutawa. Sayd ma hutun yake buqata dan haka abinci kadai yaci ya shige shima. Ita kam sbd murna yau shirin takeji da mama dan haka a jikin maman ta kwanta tana bata labari kala kala hardana Kyakkyawar lady din data hadu da ita. Yanda take yawan fadar Kyau da class din Ladyn ya saka Mama tsokanarta da cewa "To kodai Wannan karan Falaq Aziz taga wadda zata iya bari uban nata ya aura?? Shiru tayi tana sake tino Fuskan jannah din da yanda take magana muryanta ba hayaniya amma kuma tace wani yafi daddynta kyau dan haka ta girgiza kai sa sauri tana bata fuska tace "She's good amma No daddyna bazai aureta,baya sonta tace wani yafisa kyau kuma tamun tsawa kuma daddyna yafita komai,bana sonta kwata kwata ma" Fiddausi dake son shan labarin tace "To inda batai miki tsawan bafa ai da kilan tanada chance ko?? "Kallan Fiddausin tayi tana jikin maman har lokacin tace "Eh kila,amma dai No" Mama da zancen ya fara isarta tace "To indai kin fara tinanin zaki bari uban naki yai auren ai anyi arziki tinda haka ya zaba na biye shirmen banza da tinanin wadda bama hankalin ne da ita cikakke ba" Falaq bata fuska tayi tana kokarin tashi ta kalli maman tayi magana Maman ta hanata tashin tana cewa "Kina cemun witch ko oldLady zanyiwa bakinki mugun dukan da saiya fashe yayi tsawonda sbd muninsa ma ko Babanki bazai ganeki ba" Shiru tayi tana sake bata fuska qasa qasa tace "Cewa fa kikai banda hankali kwata kwata kuma kice zaki fasa mun baki,to ni ya zanyi" Fiddausi dake hana dariyarta fita tace "Mudai tinda an samu wadda ta burge Falaq Aziz a hakanma munyi arziki, Kuma zan so na ga wannan din data burge ki" Murmushi tayi tana cewa "Banfa nuna mata hakan ba sbd kada taji dadi so kar kiyita fada ma taji" "To ni ina zan ganta ma bare na fada taji amma dai zamu so ganinta ni da mama" "Ku cireni a shirmenku bana ciki" mama ta fada tana zare qaramar veil din datake nade da kan Falaq din da ganin kanta daya isa sabon gyara. Firarsu sukaci gaba da yi itada Fiddausi dake biye mata kamar qaramar yarinya suyita shirme da muguwan wasa shiyasa Fiddausin ta samu matsayi me kyau a familyn sbd yanda take saka Falaq nishadi hakama Falaq din tana sonta sosai. Da daddare bai fito cin abincin dare ba acan aka kai masa fruits kawai da dabino masu kyau da baa rabo dasu a gidan sbd shi yana cinsu sosai musammam da black tea yake cinsu masu kyan da tsafta sosai. Babu wanda ya sake ganinsa sai washe gari daya fito breakfast sanye cikin kyan sanyi sbd mura ce tai masa kamu me kyau sbd kwanan sararin da yayi a tafiyar tasu dan hakan nema ya dakatar da komai baya buqatan komai sbd ciwon kai ta sakar masa sosai. Suna gama breakfast ya nufi office din gidan da Sayd dayaketa kulawa da schedules dinsa. Zaunawa yayi yana sauraron bayanan Sayd dayake masa akan Sabon sakon ZAADENs daya taho na wannan karan Maheer Zadeen ne ya nemesa da kansa yanason zuwa da kansa dan ganinsa. Numfashi me sanyi da nutsuwa ya sauke yana cewa "Zuwa nxt month ka duba menene suke nema, Yanzu banda time na hakan. Yaya result da Baba Alhassan sun shigo? A sauya masa likita. "Ok insha Allah, Zaadens dinma already na gama bincika komai akansu tin lokacinda suka fara turo request dinsu and they seems to be clean" Batareda ya dena karanta abinda yake karantawa na report din wani project dinsu yace "Zuwa nxt month sai muyi maganar amma yanzu inda abinda yafi koma me sukeso mahimmanci" Tattaunawa sukaci gaba da yi har tsawon lokaci kafin suka fito. Da yamma fita yayi tareda falaq din sai dare suka dawo, Koda suka dawo dr na gidan yana jiransu Sayd ya riga ya kirasa. Shi aka fara dubawa kafin aka duba falaq din dan itama yasan ta debo sanyi duk da bata mura amma dai ya saba sam baya wasa da lafiyarta. Kwana biyu ya bawa falaq dasu mama time dinsa sosai kafin yayi tafiya tareda Sayd dan haka Dole mama da falaq din aka koma shiri tinda baya nan maman ce yanzu me lallabata. Kullum Fiddausi ke tayata shirin school driver ya kaita ya dawo da ita Da rana islamic/Arabic teacher dinta tazo suyi karatu har yamma kafin ta zauna waya da daddynta dare na yi suci abinci suyi dan hayaniya da Fiddausi tukuna tai bacci. Haka rayuwarta ta taso haka take dan hakanne ta saba daga ita sai familynta take rayuwa ba wani shiga mutane sosai. Duk sati biyu ake kaita gyaran kai saloon dan haka wannan satin ma shiryawa sukai Fiddausi ta fito a shirye dan itace me kaita suka nufi mota suka shiga mama tai musu a dawo lfy. Driver ke jansu suna baya suna kallan wani abu a wayar Fiddausi Falaq din na kwance jikinta suna dariya kamar daga sama sikaji wani irin qara tareda wani burki me karfin gaske daya saka falaq din samu wani irin firgita. Cikin sauri Fiddausi ta rungumeta tana kallan gabansu. Cikin sauri shima drivern ya juyo yana kallan falaq yana cewa suyi hakuri accident ne suka tashi yi amma Allah ya tsare. Falaq shiru tayi zuciyarta na bugawa da karfi sedai bata iya cewa komaiba ta lafe a jikin Fiddausi wadda itama ta tsorata sosai. Qarasawa sukai saloon din yayi parking suka fito suka qarasa ciki daidai Jannah itama tai parking a gurin ta fito sanyeda doguwar maroon arabian gown da silk scarf a kanta sai handbag dinta da wayarta dake hannunta ta nufi ciki suka shigo kusan a tare. Itace ta fara ganin falaq ta miqa hannunta zata tabota sedai hannun nata bai qarasa sauka akan falaq din ba falaq ta yanke jiki a gurin ta zube qasa. Cikin matsanancin tashin hankalin da Fiddausi bata taba shiga ba ta zube qasa tana kamo falaq din wadda idanuwanta basu rufe ba sedai kokarin rufewan suke tana qanqame hannun Jannah data kama hannuwanta itama cikin tsananin tashin hankali da tsoro. #MAMUH ZAFAFA BIYAR KALBIM 500 mamuhgee A DUNIYATA 500 Huguma AJIYA A DUHU 500 Billyn Abdul KIRJIN ME HANKALI 500 Miss xoxo Pay at 0022419171 AccessBank Maryam sani gummi Shedan biya 09033181070 Or mtn vtu at 09032345899*_Arewabooks@Mamuhgee_* 35 *KALPANAH COLLECTION* 08105064494 Shin ke daliba ce ko kuma uwa wadda har yanzu bata daina rokon urgent 2k a wurin yan uwa da kawaye ba,tou nesa tazo kusa domin kuwa na kawo miki maganin matsalarki,domin kuwa *Kalphanah Collection* ta shirya tsaf domin taimaka wa duk wani dan kasuwa ko kuma wanda yake son fara kasuwanci.A *Kalphanah Collection* muna saida kaya kama daga Jaka,Takalmi,Atamfa,Laces,Kayan yara da kuma kayan kitchen.Wani abun mamakin ma muna saida kayan mu ga masu siyen daya ko kuma sari,ga waenda basuda jari ma mun tanadar masu hanyoyi daban daban da zasu fara neman na kansu.Hajiya kina gida kwace zaki dinga jin saukar kudi a asusun bankin ki.Ga musu fuskantar qalubale a kasuwancin su kuma an kawo muku sauqi domin kuwa an bude muku group dinku da zaku dinga tattauna matsalolin ku. https://chat.whatsapp.com/JMSe2The4Q2F5tLdzGduyC Kedai idan kin shirya ki dannan link din nan na kasa domin shiga group dinmu ki ganewa idonki kunsan ance gani ya kore JI Karki yadda ki wuce bakiyi joining group din nan ba domin kuwa yanzu sallah tana qaratowa ko bakiyi kasuwanci ba zaki siya domin amfanin ki na yau da kullun kuma ko baku buqata yanzu nan gaba zaku iya neman ta. Siyen na gari maida kudi gida. 08105064494 ********** Fiddausi ce take kiran sunanta da karfi jikinta na daukan rawa sosai tana rikicewa sbd abu ne da bai taba faruwaba tinda falaq din tazo duniya hakama tsoro da tashin hankalin fuskantar AZIZ LIMBA ne yake neman zautata dan haka ta qarasa rikicewa tana girgiza falaq din koina tana kiran sunanta. Jannah ma sosai ta shiga tashin hankalin sbd itama kwata kwata bata saba da ganin irin wannan rikicewan lokaci daya ba da kuma ganin falaq din a zube. Kokarin fara kwantarwa da Fiddausi hankali tayi tana cewa ta nutsu tukuna. Ma'aikatan gurin da suka san falaq sosai tini sukai saurin fara kiran ambulance dan bata taimakon gaggawa. Jannah ce ta zare hannunta cikin na falaq din da kamar rai ya fita a jikinta ta kamota daga jikin Fiddausi dake neman kamuwa da ciwon zuciya sbd tashin hankali da tsoro. Jikinta ta kwantar da ita tana shafa fuskanta tana karanto mata adduoi tana kallan kofa da fatar Ambulance din tazo kan lokaci. Fiddausi data kasa hakura a rikice ta miqe tana cewa "Bazan iya jiraba muje asibitin kawai, Muje,muje asibitin i can't take the risk na jiran se lokacinda ambulance tazo, Pls pls mu tafi nidai... Yanda take magana a rikice bata tsayawa jin komai ya saka Jannah daukanta cak gaba daya duk da tai mata nauyi. Fitowa sukai driver dake zaman jiran gamawansu yana ganin fitowarsu da falaq din kamar ba rai a jikinta mugun faduwa shima gabansa yayi ya taso daga inda yake zaune da sauri yana nufosu ko isowa baiyiba Fiddausi data kasa magana da hannu ta nuna masa mota ya juya da gudu ya taho da motar gabansu suka fada dukansu har jannah din wadda Fiddausi ta riqeta tana rokon kada ta tafi sbd tsoro takeji kar abarta da Falaq din ita kadai zuciyarta zata iya bugawa sbd tashin hankali da fargaba. Yanda ta roketa da yanda itama zuciyarta ta kasa barin Falaq din wannan halin ya sakata binsu suka nufi asibiti tana goga tafin hannun falaq din da sauri sauri ko zata farfado amma sam ko zuciyar falaq din bata bugawa ko kadan. Kafin su isa asibiti hannuwan Fiddausi rawa sukeyi sosai tana kokarin controlling kanta ta ciro wayarta a jaka ta nemo sunan Mama ta saka kiranta tana sauke numfashi me karfi dayake dan yankewa. Mama na daga wayar kannewa tayi tace "Mama muna hanyar asibiti falaq ce, Bansan meya sameta ba ta fadi bata motsi,bansan meya faruba,bansan yaya akaiba.... Kasa riqe jarumtar tayi ta qarasa zancen muryanta na karyewa da yanayi me damuwa sosai. Mama ma kanta ne taji ya sara ta zauna daga tsayen datake tana cewa "Innalillahi wainnna ilayhi rajiun, Ita falaq din? Kuna isa ki turomun location ganinan tafe yanxu kuma karki sanar da Sayd sbd kada AZIZ ya sani tukuna" Kashe wayar Fiddausi tayi sbd sun iso asibitin. Ciki akai da ita da sauri sukuma suka zauna waiting area bayan ta turawa mama location din tana kai da kawo kama zata shiga taji menene ya sameta. Jannah kuwa jin tayi itama fargaba da tsoro haka kawai yana shigarta, Jin take kaman wanzuwarta a gurin bai kamata ba amma kuma ta kasa tafiya sbd haka kawai tausayin yarinyar ke rufeta sbd tana tinawa da lokacin da kuruciyanta take gaba daya a yawon asibiti ta qareta. Kanta taji yana neman juyawa sbd tinanin halinda ta taso rayuwarta da babu komai a cikinta sai ciwo da kadaici da qunci, Dafe kirjinsa tayi sbd bugawan da zuciyarta tafara da karfi tana harbawa. Jakarta ta bude ta ciro maganinta ta bude tayi saurin sakawa a bakinta ta hadiye tana rufe idanuwanta da suka fara cikowa da hawaye sbd itama ciwonta data fito ya zamar mata tamkar trauman da bata iya tinawa sai ta shiga wani hali. Hankalin Fiddausi bai tashi ba saida aka dauki lokaci baa samu falaq ta farfado ba doctors na shiga serious bincike akanta. Mama ma data iso samun ba wani bayani akan hakan hankali tashi yayi. Muryan data sakata juyowa ne ya sauka kunnenta ana cewa "Ina wuni" Jannah din ta zubawa ido tana jin yanayi kaman na sani akan jannah din sedai kuma bata taba ganin fuskanba dan haka jikinta na sanyi ta amsa gaisuwan tana mata godia akan kawo falaq din asibitin. Jannah dataji tsananin tausayi da mutuncin Dattijuwar ya shigeta girgiza kai tayi ahankali tana sunkuyar da kanta daga kallan fuskan maman data cika mata ido da yanayi me sanyi da kauna haka kawai idanuwanta na cikowa da hawaye ta juya da sauri tana maidasu. Acan gida mama na fita motar data daukosa daga airport tana shigowa dan haka suna shiga securities suka sanar dashi maman ce ta fita yanzu da mota. Shiru yayi batareda ya dagoba daga wayar dayake dubawa sedai ya dakata daga abinda yake. Sayd ne ya kalli gurin ajiye motacin gidan yaga babu motar Falaq da ake fita da ita yace "Falaq fa? "Ms Falaq sun dade da fita itada Fid" Sai a lokacin LIMBAn ya dago idanuwansa ya kalli Sayd wanda take ya ciro wayarsa ya saka kiran wayar mama wadda taketa ringin bata daukaba. Ciki sika qarasa kai tsaye bangarensa ya nufa ya ajiye wayoyinsa ya fada wanka dan sauya kayan jikinsa. Bai jima ba ya fito sanye da sweatset Off-white na Prada qamshinsa na na tashi a hankali ya dauki wayarsa ya saka kiran maman da kansa. Ringing ta fara harta yanke baa daukaba. Ajiyar zuciya me dumi ya sauke ahankali yana kallan time idanuwansa na sauyawa a natse. Rayuwarsa abu dayane kowa ya sani ya tsana kuma yakewa tsananin qi wato ya kira na gida aki daukan wayansa sbd da hakanne aka boye masa ciwon Ummitah data rasu batareda yazo ya ganta ba, Ummitah ta dade tana ciwon da aka boye masa wanda ya saka idan ya kira baa dauka sbd kada ya sani, Hakama Ummitah ta rasu kowa ya dena daukan wayarsa sbd kada a sanar masa har Ummitah tai kwanaki da rasuwa yana duniya da rai da lafiya amma bai taho ga koda gawarta bane duk akan rashin daukan wayansa hakanne ya saka duk duniya baida abin qi da mafi tsana irin ya kira aqi daukan waya sai kuma Nigeria daya yanke zuwa gaba daya sbd baida komai da kowa a cikinta. Dan hakanne ya saka kwata kwata duk wanda ya sansa baya wasa da rashin daukan wayarsa, Business koda na billions ne idan ya kira kaki dauka to ko waye kai ya gama Business dakai koda zai rasa billions din shima kuwa shiyasama kwata kwata bai cika kiran mutane ba sedai a kirasa kokuma Sayd da kusan shine yake kulawa da duka calls dinsa sbd sunsha rasa manyan kudaden gaske akan wannan akidar tasa da kuma dole kowa yake binta. Kaf duniya mama ce kadai take masa rashin daukan waya batateda fushi ko bacin ransa ya bayyana sbd kasancewanta uwa dan haka yanxu dinma bai sake kiranta ba Wayar Sayd ya saka kira. Sayd dayake fitowa wanka yana ganin kiransa ya daga yace "Yes" "Ina buqatan location na inda Falaq Aziz take zan daukota da kaina" ya fada a taqaice yana kashe wayar ya ajiye gefensa. "Ok yes" sayd ya fada yana nemo numbern Fiddausi ya saka kira. Fiddausi na ganin kiransa kanta y sara ta dafe goshinta jikinta na sanyi ta daga kiran sbd bata isa qin daukan wayarsa ba tana aiki a karkashinsu kuma kiransa kaman kiran LIMBA ne da kansa dan shine yake isar da sakon duniya kowanne iri ne na LIMBA. Tana dauka ta bude baki zatai magana ya katseta da cewa "Turomun location naku right now LIMBA is coming" Dago jajayen idanuwanta tai ta kalli mama wadda take zaune ta zubawa jannah idanuwanta cikin nutsuwa tana kallanta sedai damuwa ce a zuciyarta fal gashi tana kallan kiran AZIZ ta kasa dauka sbd batasan ta sakasa damuwa kuma tasan rashin daukan waya shine babban asalin bacin ransa. Kashe wayar sayd ya saka dukkanin jikim Fiddausi sanyi ta tura masa location din sbd batada yanda zatai kuma dai ciwon Allah ne ya kawo kaddarars koma menene daman tsoronta kada ace ganganci tai bata iya bawa falaq din kulawaba. Tana tura masa ta kashe wayarta ta ajiye gefe tana dafe goshinta tareda sauke numfashi da ajiyar zuciya a tare. Sayd na samun location din cikin mintina kadan ya shirya ya fito qamshinsa me tsada yana tashi sanye da three quarter da riga na Burberry milk da key a hannunsa da wayarsa. Fcap LIMBA ya fito da ita sanye yana kashe wayarsa gida dan bawa falaq time dinsa a hanyar dawowansu gidan duk da zuciyarsa gaba daya tana karban rashin nutsuwa ne da falaq din kawai yake buqatan gani. Sayd sam bai lura da location dinba saida suka shiga mota ya tayar yana budewa yaga asibiti ne. Shiru yayi tareda juyowa ya kalli AY dayake shigowa a natse ya zauna. Jan motar yayi baice komaiba suka nufi asibitin. Saida suka shiga asibitin yayi parking tukuna AY ya dago ya kalli asibitin kafin ya kalli Sayd kafin yayi magana idanuwansa suka sauka akan motar Falaq sai kuma ta mama duk a guri daya. Baici komaiba aka bude masa motar cikeda girmamawa ana cewa "Welcome boss" Ryan ne drivern Falaq din dayake zaune a cikin damuwa shima yana ganin motar ya taso. Kafafunsa ya ziro waje yana fitowa Sayd ma fitowan yayi yana rufe motar suka nufi ciki Ryan na cewa "Ms Falaq Aziz is... Bai fada abinda zai fadaba Sayd yayi masa alamar yayi shiru kawai sbd LIMBAn da yasan a yanzu daya riga ya gama sanin Falaq ce a asibiti baya buqatan jin bayanin kowa saina likitoci kawai. Fiddausi da mama ne suka juyo a tare suna kallan hanyar daya sako kai sbd qamshin BLACK VIOLET daya ratso gurin cikin sanyi take suka san shine yake tahowa a natse ya tinkarosu sayd na gefensa Ryan ba bayansa. Sunkuyar da kai Fiddausi tayi cikin girmmawa tana bude bakinta a natse tai masa barka da dawowa. Mama fuskansa da kowannensu ya kasa karantar halinda take ciki ta kalla tana cewa "Barka da dawowa, Sayd ta kalla dayake gaidata ta amsa gaisuwansa tana maida kallanta akan AZIZ din daya gaidata kai tsaye ba tareda bayyanar da yanayin komai da komai dagewanka bazaka iya cewa ga yanayinda yake ciki ba ya wuce kai tsaye gurin likitan daya bude kofar emergency room din yana fitowa Nufarsa kofar yayi daidai da juyowan Jannah dake waya tin dazu a natse da murynata mara hayaniya. Tana juyowa yana kawowa gefenta wanda qamshinsa ne ya fara shiga hancinta daya sakata dagowa daidai isowansa gap da ita sedai ko alaman yasan da mutum a gurin baiba sbd fararen idanuwansa dake akan dr din daya fito ya rabeta ya wuce. #MAMUH ZAFAFA BIYAR KALBIM 500 mamuhgee A DUNIYATA 500 Huguma AJIYA A DUHU 500 Billyn Abdul KIRJIN ME HANKALI 500 Miss xoxo Pay at 0022419171 AccessBank Maryam sani gummi Shedan biya 09033181070 Or mtn vtu at 09032345899*_Arewabooks@Mamuhgee_* 36 *KALPANAH COLLECTION* 08105064494 Shin ke daliba ce ko kuma uwa wadda har yanzu bata daina rokon urgent 2k a wurin yan uwa da kawaye ba,tou nesa tazo kusa domin kuwa na kawo miki maganin matsalarki,domin kuwa *Kalphanah Collection* ta shirya tsaf domin taimaka wa duk wani dan kasuwa ko kuma wanda yake son fara kasuwanci.A *Kalphanah Collection* muna saida kaya kama daga Jaka,Takalmi,Atamfa,Laces,Kayan yara da kuma kayan kitchen.Wani abun mamakin ma muna saida kayan mu ga masu siyen daya ko kuma sari,ga waenda basuda jari ma mun tanadar masu hanyoyi daban daban da zasu fara neman na kansu.Hajiya kina gida kwace zaki dinga jin saukar kudi a asusun bankin ki.Ga musu fuskantar qalubale a kasuwancin su kuma an kawo muku sauqi domin kuwa an bude muku group dinku da zaku dinga tattauna matsalolin ku. https://chat.whatsapp.com/JMSe2The4Q2F5tLdzGduyC Kedai idan kin shirya ki dannan link din nan na kasa domin shiga group dinmu ki ganewa idonki kunsan ance gani ya kore JI Karki yadda ki wuce bakiyi joining group din nan ba domin kuwa yanzu sallah tana qaratowa ko bakiyi kasuwanci ba zaki siya domin amfanin ki na yau da kullun kuma ko baku buqata yanzu nan gaba zaku iya neman ta. Siyen na gari maida kudi gida. 08105064494 *************** Kasa motsawa tai daga inda take tsayen hakama iskan qurin ta sauya gabaki daya da qamshin data tabbatarda nasa ne sbd shine ya doki hanci da fuskanta a lokacinda ya wuceta batareda yasan da akwaita bama, A rayuwarta kaf tinda ta taso bata samun kanta a inda aka taba nuna baasan da existence nataba, Idan baa kulata da bata kulawa tareda nuna mata mahimmanci ba sbd Sunan familynta to zaayi sbd dukiyar datake dashi kokuma sbd kyau da daukan ido datake dashi amma a karo na biyu an nuna baama san da matsayinta n yar adamba kuma duka daga mutum daya. Tsananta bugawa zuciyarta keyi hakama ta kasa juyowa ta kalli bayanta da dukkaninsu suka nufa dan bin bayansa zuwa ga doctor. Muryansa daya ambaci sunan doctor dashine a wani irin nutsuwa ya saka numfashinta fita da wani irin tsananin sanyi daya sakata juyowa ahankali sedai ta kasa kallansa sbd yanda zuciyarta ke bugawa. Juyawa tayi tabar gurin tana fitowa harabar gurin sbd jin tai tana suffocating. Tana ji wayarta na ringing kuma tasan Ammar Zad ne amma bata iya dauka sbd nunfashinta toshewa yake haka kawai sbd bugawan da zuciyarta keyi. Ringing wayar taci gaba dayi amma sam bata iya ko dauko wayar daga handbag dinta. Taxi ta tare ta fada tabar asibitin ta koma saloon sbd motarta nacan ta baro. Doctor kuwa kallan AZIZ din yayi yana sauke ajiyar zuciya me tsananin sanyi da nutsuwar abinda yake son fada masa kafin ya bude baki yace "Muna saka ran zata farfado kowane time sedai a abinda muka bincika ya kawo mata collapsing shine ta samu bugawan zuciyan da yayi triggering matsalan datake dashi a zuciyanta wanda muna jiran fitowan sakamakon duka binciken da muka fara yi mata na dan abinda muka gani tukuna."" Shiru gurin ya dauka sbd babu wanda ya motsa a cikinsu kallan likitan suke kamar basu fahimci abinda ya fadan ba dan haka ya kallesu shima likitan daya bayan daya tukuna ya tsayar da kallansa akan AZIZ da shima bayanin yake buqatan sake ji sbd a lamarin daya shafi iyalinsa yanason a ringa masa dalla dalla. Ganin hakan dr ya sauke ajiyar zuciya yace "Mun dan gano tanada matsala a zuciyarta sbd yanayin bugun zuciyar nata da muka duba vayan dawowansa ba bugun zuciya bane na cikakkiyar lafiyayya, Bai taba bayyana va sai yanzu data samu bugun zuciyan dayayi munin daya bayyanarda ciwon gaba daya, Amma muna jiran sauran result da kuma wainda zamuyi mata dan tabbatarda komai" Hawaye ne masu tsananin zafi suka tsinkewa Fiddausi suna gangarowa akan fuskanta tayi baya tana komawa nesa dasu ta zauna tana cusa kanta cikin kafafunta. Mama kuwa gaba daya bata gane turancinba dan haka sayd da AY din take kalla tana jiran reaction dinsu ya bayyanar mata lafiya ko ba lafiya ba. Sayd wani irin nauyi ne ya danne kirjinsa da daci dayake gauraye bakinsa gaba daya idanuwansa na sauyawa sedai bai bari hakan ya bayyanaba ya danne tareda dagowa ya kalli AZIZ AY LIMBA wanda kafafunsa suka so kasa daukansa duk jarumtarsa. Saurin taresa mama da sayd din sukai tare ya kasa dago idanuwansa ya kalli ko dayansu sbd yanda sukai jajir a take cikeda mafi girman 'dacin zuciya da wani irin nauyin daya danne kirjinsa da babu komai a cikinsa sai fili da tarin quncin daya taso a cikinsa. Kujeran aka kawo masa da sauri ya zauna har lokacin bai iya dagowa ba bare iya cewa komai. Sayd ne ya kalli dr din da jajayen idanuwansa da suka sauya sosai shima sbd su bazaka iya controlling nasu ba ya bude baki yana kokarin daidaita kansa yace "Ok dr zamu jira results din da duka sauran bayanan,thank you" Juyawa dr yayi ya koma ciki tareda nurse data fito kiransa. Shiru gurin yayi babu wanda ya iya magana sai sayd da mama take sake tambayar ayi mata bayanin meya samu Falaq din sbd itama tin bata jiba ganin yanayinsu ya sakata jin ciwon zuciyarta na neman tasowa dan kirjinta toshewa yafara yi fargaba na shigarta me girma. A taqaice sayd yayi mata bayanin abinda aka fadan yana dorawa da kada ta damu insha Allah khairan. Duk yanda taso daurewa kasawa tayi kirjinta ciwo yake mata dan haka Fiddausi dake kuka sayd ya saka ta kawowa maman ruwa ya bata yana cewa nurses su kira doctor ya dubata. Yanda ya zauna baice komaiba shiru yayi sukaci gaba da zaman jira. Sallah sukaje sukai suka dawo cigaba da jira amma ba wani zance karshe dai an fito da falaq din zuwa vip room dayake can sama dan haka suka koma can. Shiru dakin babu maganar komai sbd uban gayyar baicewa kowa komaiba har lokacin farfadowan falaq din yake jiran gani tukuna har doctors din ya samu magana dasu kafin su wainda suke tareda ita da abinda ya faru. Mama dai dole aka maidata gida sbd duk ta rikice jikin nata ya tashi dan haka gida aka maidata gida tareda Fiddausi ma da nurse da sayd ya daukan mata. AZIZ dinne ya kwana a asibitin a zaune sai sayd da shi duk inda ko inuwar AZIZ take yana nan. Guraren 8 na safe ta farka cikin tsananin sanyi da rashin walwala ta ciwon daya sauyata a lokaci daya. Tana bude idanuwanta akan Daddynta ta fara saukesu hawaye masu dumi suka gangaro mata ta gefen fuskanta ta bude baki Ahankali tace "BestDaddy" Har cikin ransa yaji saukan sanyin muryanta wani irin daci da qunci yafara cike koina a zuciyarsa ya bude idanuwansa da suka kasa komawa daidai ya zuba mata yana tayar da ita zaune ahankali yana dora hannunsa akan fuskanta ya shafa ya bude baki da muryansa me nutsuwa yace "Hey Falaq Aziz limba,how are you feeling? Wasu hawayen ne suka gangaro mata ya ciro handkerchief dinsa yana goge mata ahankali yace "Yaya dai?kina jin ciwo ne? Where?a aina? Kwantawa tayi jikinsa tana girgiza masa kai alaman batajin ciwo koina. Dr ne ya shigo ya qara dubata dakyau kafin yace zuwa anjima ma zasu iya tafiya gida ba damuwa ko matsala bane. Angama dube dube da sauran duka test da full checkup da AZIZ yace ayi mata sbd yanason a bayyane masa komai daya danganci abinda yake damunta komai yanason a bincika a sanar masa zai nema mata lafiya indai Allah ya yadda ta samu lafiyar koda zai rasa komai daya mallaka. Koda suka dawo gida gabaki daya babu wata walwala ko haske ko kadan a tattare dashi suma duka gidan jikin kowa a mace yake sedai sbd falaq din su Fiddausi da mama suka sake sunata kulawa da ita da wasa dan ta sake kuma tafara sakewan sbd rashin qarfine kawai na wuni da kwana a kwance yake Damunta sai kuma asalin weakness da ciwon yake sakarwa meshi datake ji. Doctors sun sanar dashi results da binciken duka suna kammaluwa zasu kirasa yazo ayi masa bayanin komai dan haka duka schedules da ayyukansa na wannan lokacin ya saka sayd yayi cancelling nasu ya bawa falaq time dinsa sosai wanda hakan ya sakata komawa daidai rigimarta da komai ya dawo musamman dataga mama ta dena mata fada dan haka murna ta ringa yi da ciwon datai. Ryan kuwa tini ya sallamesa aka daukan mata wani drivern bayan an sanar dashi daga lokacinda yayi wani gangancin da ita a mota ya gama aikin. Shi da Sayd ne a cikin damuwa sosai akan tinanin ciwon nata wanda basu gama sanin yaya yakeba dan haka koyaushe cikin jiran kiran doctors yake hakama sayd Ciwone yake cinsa na tsakanin Uba da 'ya tinda aka fada ciwon sedai kawaicinsa da yanda yabarwa AY ita bai nuna damuwarsa a fili ba dan haka ya fara bibiyan bayanan ciwon zuciya da matsalolinta. Ganin hakan sai mama ma suka nuna mata ba wani damuwa bane falaq will be ok insha Allah, Da wannan maman ta sake itama ta koma yanda take. Tinda ya taso bayan rasuwar mahaifinsa zuciyarsa tafara bushewa daga mutane da lamarin duniya, Ya rasa Mahaifiyarsa zuciyarsa ta karbi hakan cikeda jarumta da taurin zuciyar daya reni qanwarsa dashi, Ya rasa Ummitah dayafi so a duniyarsa fiyeda komai da kowa zuciyarsa ta rasa duk wani emotions daya wuce na falaq, Ba masu fada ba shi kansa yasan zuciyarsa a bushe take shiyasa a duniyar tycoons ake kiransa da monster amma baisan meyasa yakejin zuciyarsa na neman karyewa akan ciwon dayake tafe ga 'yarsa daya tak da itace kuzarin datake riqesa daga collapsing a duk lokacinda rashin Mahaifiyarta ke neman illata kwakwalwa da tinaninsa tareda jinsa da ganinsa. Rufe idanuwansa yayi Ahankali yana hadiye abinda yake cikeda zuciya da kirjinsa. Sayd ne yai knocking ya bude kofar palon y shigo a natse yazo gabansa ya tsaya cikin girmamawa da nutsuwa yace "Hospital sun kira the results are out da komaima" Bude idanuwan yayi Ahankali tareda zubasu akan sayd din wanda ya sauke nasa idanuwan. Shiru gurin y dauk kafin ya miqe yana daukan wayarsa dake gefensa yana cewa "Lets go" Bayansa sayd yabiyo yana zuwa inda keys din motocin gidan yake ya dauko key yana biyosa da sauri. Mota suka shiga zuwa asibitin batareda kowa yayi magana a motarba har suka isa. Suna isa kai tsaye office din dr A Raheem suka nufa wanda shine babba gaba daya a asibitin suna isowa shine da kansa ya budewa AZIZ din kofar shiga yana masa barka da zuwa. Amsawa yayi yana gaisawa da doctors biyu dake dakin wainda manyan neurologist ne wanda sune zasuyi masa bayanin duk abinda ya shafi ciwon yarsa. Shiru office din yayi bayan Dr Raheem ya gabatar masa dasu fara koro bayaninsa yayi cikin tsananin nutsuwa. "Mr LIMBA kaman yanda aka fara sanar da kai tabbas 'yarka na dauke da ciwon rashin qwarin zuciya wanda dashi tazo duniya sedai baya nunawa sbd the more tana girma the more yake kokarin fara bayyanarda kansa, A yanzu ya bayyana ne sakamakon shock ko mummunan bugawan zuciyar data samu, Ciwone chances din warkewansa yake 20% Zaici gaba ahankali ahankali zuwa lokacinda zuciyarta zata buqaci heart transplant maana dashen zuciya kafin tata ta iya dakatawa, Ciwon wasu yakan zo musu da rami ne a zuciya kaman hole haka".... ya fada yana kunna musu qatuwar screen din dake office din yana nuna musu yanda ciwon yake. #MAMUH ZAFAFA BIYAR KALBIM 500 mamuhgee A DUNIYATA 500 Huguma AJIYA A DUHU 500 Billyn Abdul KIRJIN ME HANKALI 500 Miss xoxo Pay at 0022419171 AccessBank Maryam sani gummi Shedan biya 09033181070 Or mtn vtu at 09032345899*_Arewabooks@Mamuhgee_* 37 *KALPANAH COLLECTION* 08105064494 Shin ke daliba ce ko kuma uwa wadda har yanzu bata daina rokon urgent 2k a wurin yan uwa da kawaye ba,tou nesa tazo kusa domin kuwa na kawo miki maganin matsalarki,domin kuwa *Kalphanah Collection* ta shirya tsaf domin taimaka wa duk wani dan kasuwa ko kuma wanda yake son fara kasuwanci.A *Kalphanah Collection* muna saida kaya kama daga Jaka,Takalmi,Atamfa,Laces,Kayan yara da kuma kayan kitchen.Wani abun mamakin ma muna saida kayan mu ga masu siyen daya ko kuma sari,ga waenda basuda jari ma mun tanadar masu hanyoyi daban daban da zasu fara neman na kansu.Hajiya kina gida kwace zaki dinga  jin saukar kudi a asusun bankin ki.Ga musu fuskantar qalubale a kasuwancin su kuma an kawo muku sauqi domin kuwa an bude muku group dinku da zaku dinga tattauna matsalolin ku. https://chat.whatsapp.com/JMSe2The4Q2F5tLdzGduyC Kedai idan kin shirya ki dannan link din nan na kasa domin shiga group dinmu ki ganewa idonki kunsan ance gani ya kore JI Karki yadda ki wuce bakiyi joining group din nan ba domin kuwa yanzu sallah tana qaratowa ko bakiyi kasuwanci ba zaki siya domin amfanin ki na yau da kullun kuma ko baku buqata yanzu nan gaba zaku iya neman ta. Siyen na gari maida kudi gida. 08105064494 ******** Screen Sayd ya zubawa idanuwansa yana kallan yanda ake nuna musu cutar take a zuciyar dan adam. AY idanuwansa da sukai jajir har suna radadi ya zubawa dr din kunnuwansa na ji masa mummunan labarin dayafi rasa komai da komai daya mallaka muni. Dr kuwa cigaba yayi da cewa "Zaa dorata akan activities da zaa fara kiyayewa da dorata akai tin yanzu batareda an daga mata hankali tasan meyake damuntaba dan tayi qanqanta data san hakan kuma sbd Nata baiyi nisan da zaa cire rai ba sedai kuma bamusan abinda gaba zatai ba wadda idan har ankai stage din da baaso to sai anyi mata heart transplant din wanda samun donor shine abinda yakeda wuyar datafi komai a duniyar nan" Hotuna da videos na yanda ake heart transplant ya kunna yana cigaba da musu bayani cikin kwantar musu da hankali da kokarin ganin ya fahimci komai tareda sanin ba wani abu ne me mugun tashin hankaliba sbd ciwonta baiyi nisa ko girman da zai gagaresuba insha Allah. Sayd dagowa yai ahankali daga jinginen dayake yana saukar da idonsa da kyau akan hotinan dake yawo akan babban screen din na heart transplant da asalin tabon dayake bari a kirjin da duk aka cire zuciyar ko dasata. Kasa dauke idanuwansa yayi daga hoton wanda ya saka kunnuwansa daukewa daga jin sautin bayanin da doctors keyi sbd mamaki me tsananin gaske da shock dayake neman shigarsa sbd sanin wannan shine irinsa sak a kirjin Ummitah wanda bai taba saninta dashi ba dan ko ranar da zaa kaita asibitin haihuwa shine ya saka mata kaya da kansa dan bazata iya ba kuma babu wannan dinkin a kirjinta sai bayan rasuwarta ya gansa. Juyawa kansa ya farayi sedai kuka Cs akai mata aka ciro Falaq, Ana cs na haihuwa a kirji ne?? Girgiza kansa yayi idanuwansa na sauyawa yana kokarin tina babu dinkin cs da akai mata a mararta. Jin yayi ya dena gane komai kansa na yin dum.. Jajayen idanuwansa da suka sauya gaba daya a take ya kalli dr Raheem ya bude bakinsa muryansa a shaqe yace "Dr a wane gefe na kirjin ake aikin? A jikin dan adam akwai inda zaa iya masa tiyata a cire 'da bayan cikin? Meye dinki a kirji kuma a bangaren hagu yake nufi?? Kallansa dr yayi yana mamakin tambayarsa AY kuwa sam bayama cikin cikakkiyar hayyacinsa na fahimtar me Sayd din yake tambaya yana zaune shiru idanuwansa sunyi laushinda ayau zaka gane rauninsa a bayyane. Cikin bude masa komai da kyau dr yace "Babu inda ake iya cirewa mace baby bayan cikinta maana qasan cikinta wanda wasu ana yankan tsaye wasu kuma na kwance,amma idan har kana magana ne akan wannan yankan na setin zuciya wanda ya tafi daidai irin wannan da kake gani to idan a jikin rayayye ne akwai tabbacin antaba masa aiki a zuciyar, idan kuma matacce ne to tabbas shima anyi masa aikin ne a zuciya kokuma ma an cire zuciyarne tinda a macen yake" Jiri ne ya dauki Sayd daga zaunen da yake sbd kansa kasa gane komai yai Jin yake kamar bai taba zama aji karatu ba sbd jin yayi turancin ma kamar ya dena ganewa dan haka ya juyo idanuwansa da sukai nauyi sosai ya kalli AZIZ wanda shima kwata kwata jinsa yai qasa akan bayanan likitocin gameda ciwon daya bayyana lokaci daya a tattareda rayuwar yarsa wadda bayan kuruciya ma yanzu babu abinda zata gane a ciwon ko anmata bayani..... "Innalillahi wainnna ilayhi rajiun,Ya salam" Ya fada yana tallafe goshinsa da hannuwansa biyu idanuwansa na rufewa ya budesu tareda jimawa shiru kafin ya dago ya kalli kowannensu ya bude baki baki yayi musu godia tareda miqewa. Sayd ma miqewan yayi baa hayyacinsa ba sbd yayi mugun zurfi da nisa da tinanin dayake sake toshe kansa. Ta email akaiwa Sayd forwarding copies na results dinta da sauransu sbd duk inda zasu sauya ganin likita ko qasar ma zai zamana sunada record dinta. Tafiya suke babu me magana hakama babu wanda yake cikin cikakkiyar hayyacinsa har suka isa mota suka shiga kowannensu yayi shiru. Sayd kasa tada motar yayi sbd bayajin zai iya driving cikin daurewa ta juyo ya kalli LIMBA da babu abinda yake iya cewa sai yaji tsananin tausayinsa dan ganin rauninsa da karyan kowa ne yace ya gani. Jin yayi jarumtarsa ta dawo dan shine tamkar bangon dayake taresa a duk lokacinda rauninsa ya taso dan haka yake koyaushe a shirye daya basa kariya koda shi zai rasa nasa ran sbd kaunar Ummitah data hadasu haduwa ta har abada. Numfashi me sanyi da ciwo ya sauke yana dora hannunsa ya tada motar yana tattaro nutsuwa da karfin hali ya hau hanyar gida. Tafiya ce ta damuwa da rashin haske ko kadan a cikinta sukai har suka isa gida.. Suna isa kai tsaye babu wanda ya gansa ya shige bangarensa ya rufe kansa sai alokacin yaji kirjinsa nai masa radadi da ciwon daya sakasa zubewa palo qasa yana dafe kirjinsa yana lumshe ido yana karban radadin sbd babu yanda zai iya dauresa. Yana jiyo ihun falaq din da Fiddausi da dayar me aikinsu a baya suna wasan daya sakasa rintse idanuwansa yana jin inama shi Allah ya kaddarowa wannan ciwon ba Falaq ba sbd harko yaushe yana fatar kasancewa da Ummitah koda a fatalwa ne idan har zasu hadu. Falaq ce jinin Ummitah daya rage masa a duniyar, Falaq itace take rage ciwon radadin rashin mahaifiyarta daya bar zuciyarsa empty idan har ciwonta barazana ce ga rayuwarta da zata iya rasa zuciyar da itace rayuwar yaya zaiyi da wannan kaddarar da Allah daya kaddaro masa shi kadai ne zai kawo masa dauki... Zuciya ce zata buqata idan lokaci yayi wanda ba aba bace da tarin dukiyarsa zata siya, Meye amfanin kaf abinda ya mallaka idan har bazasu nemo masa abinda zai buqatan ba? Falaq dake wasan ruwa da water guns dasu Fiddausi farin ciki kawai take jin kanta yana ciketa wasa sukeyi sosai batama san daddynta ya dawo ba kuma yana jiyota radadin zuciyarsa na qaruwa duk dariyarta ta shiga kunnuwansa sbd ahankali ahankali wannan farin cikin da dariyar zasu disashe daga rayuwarsu kenan. Sai magrib suka dena wasan suka dawo ciki Fiddausi na janta daki ta sakar mata ruwan zafi sosai sbd sanyin da sukai wasa dashi karya kamata. Cikin jallabiya milk me tsadar gaske ya fito fuskansa tayi fresh sbd wankan da yayi ya fiton,. Fuskansa babu walwala ko kadan sedai sam fuskansa bata bayyanarda fushi, Sayd ne shima ya fito sanyeda riga da wandon fendi masu haske suka nufi masallaci wanda saima anyi tafiya da mota ake zuwa. Koda sukai sallan magrib basu dawoba a masallacin suka tsaya AZIZ din karatun AlQuran ya ringa yi har lokacin isha yayi akai sallah suka fito suka kamo hanyar zuwa gida. A hanyar ne ya dan kalli Sayd din a natse kafin ya maida kallansa kan Wayarsa yace "Kafin gobe a saka binciken qwararrun manyan likitocin zuciya na duniya gaba daya zan gansu" "Yes AY" Sayd ya fada yana ciro wayarsa dan fara saka binciken. Suna isowa gida ya nufo ciki yana sako kai falaq dake fitowa hanyar bedroom din mama da gudu tayo kansa tana murmushin farin cikin ganin halittar datafi mata kowa da komai tana cewa "BestDaddy" Rungumeta yayi yana sauke boyayyar ajiyar zuciya da wani lafiyayyar murmushi daya sakawa fuskansa wani irin sabon nutsuwa da kwarjinin gaske. Sayd bai qaraso ba bedroom dinsa ya nufa yana wayoyi.. Yana gama wayar ipad dinsa da tinda suka dawo asibiti yake kai yana wani irin binciken dayake neman juyar masa da kai, Gaba daya zarewa yake neman yi kawai daurewa yake sbd kada AZIZ yasan komai akan abinda baida tabbaci amma kuma ya tabbatarda dinkin kirjin Ummitah sabo ne kuma a asibitin data haihu ta samesa sbd ya sake tabbatar da cewan ranar da zasu tafi da ita koda ya saka mata kaya a jikinta babu raunin komai a jikinta bare dinki, Kuma a yanzu bayan dawowansu ya rufe kansa a daki ya kira likitocin duniya sunfi goma zance daya suke basa akan abinda dr Raheem ya fada baa taba aikin komai a kirji kuma bangaren hagu saina zuciya hakama indai mace ta haihu babu alamar tiyata a qasan cikinta koda daga gefe ne to da kanta ta haihu ba cs akai mataba. Dafe kansa yayi dayake juyawa yana neman zare masa idanuwansa sukai jajir, A ranar da aka shiga cs da Ummitah babu kowa a bangaren kaman yanda babu ko hayaniya alamar kebantaccen guri ne dayake nuna alama da vip area ne na asibitin, AZIZ baisan suna meyake faruwa ba bare yasan asibitin dasuke bare yasa a basu special treatment hakama Alh Saad baisan suna asibiti a lokacin ba sbd basu tsaya sanar da kowa ba sbd tashin hankali,,,,to meyesa aka kaisu Vip area din???? Ko sisinsu baa karba ba idan ya tina harsuka bar asibitin da gawar Ummitah........ Miqewa yai da sauri ya nufi windon dakinsa ya bude iska ta daki fuskansa ya rintse idanuwansa sbd sarqewa numfashinsa keyi yana neman zaucewa... Iska ya shaqa numfashinsa ya dan dawo daidai ya dawo da sauri ya wafci ipad dinsa yana sake bin bincikensa daki daki sedai yasan shedan ne kawai keson illata zuciyarsa da tinaninsa dan babu yanda zaayi ace anyiwa Ummitah aikin zuciya basu saniba, Kodai dataje rasuwa ne sukai kokarin hana zuciyarsa dena aiki sukai mata aikin zuciyar?? Me wannan tinanin yakeyi a kansane?? Menene yake damunsa? Wane irin jahilin tinani ne wannan yake yawo akansa?? Laptop dinsa dake bude itama yana binciken da ita ya duk ya rikice yayi da wayarsa yayi da ipad yayi Laptop ya kira waya duk ya neman haukacewa yake neman yi...... Cikin wani irin zafi ya dauki Laptop din ya bugata da qasa yana yana dafe kansa tareda zubewa a couch yana rintse idanuwansa hannuwansa na dan rawa. Numfashi yake saukewa da karfi karfi yana sauka ahankali yana kokarin dawowa daidai hayyacinsa. Bude idanuwansa da sukai ja yayi Ahankali yana dawowa da tinaninsa daidai.. Akan tinanin Abinda yake shirin faruwa tinaninsa ya tsaya da hankalinsa.. "Bayyanar ciwon falaq na Bayyanar musu abinda basu sani bane ko me? Kaddara ce ko Haske ne yake buduwa a garesu?? Numfashi ya sauke tareda miqewa ya fada toilet yayi wanka kansa ya dan sake alokacin ne ya shirya ya fito sallan magrib da suka fita da LIMBA. A yanzu da suka dawo kaman yanda AZIZ ya saka a binciko masa qwararrun doctors din zuciya shima zaiso ganawar dasu dan tabbatarwan karshe dan haka a cikin daren ya saka babban Pa dinsa da kusan daga shi sai Fahad din a kusanci da kulawa da duk kadarorin LIMBA yace zuwa gobe a hado masa list na best qwararrun cardiologist da bayanansu ya tiro masa. "Yes boss by tomorrow insha Allah komai zai iso gareka" Kashe wayarsa yayi yana kokarin daidaita kansa ya fito. AZIZ na babban palon har lokacin zaune tareda Falaq dake jikinsa tana masa labari kala kala hadda na Ladyn datake ta magana akanta duk kwanakin wadda take cewa bata burgeta ko kadan amma ta kasa dena maganarta. Tana ganin sayd gurinsa ta dawo tana fesa masa labarai kala kala yana biye mata shida mama sbd Daddynta kwata kwata baya cikin yanayi na iya biye mata sbd abinda yake cin zuciyarsa. Abinci suka ci banda AY din wanda tea da dabino kawai yaci ya shige bayan Falaq tayi bacci ta shige kenan. #MAMUH #REVENGE #LOVEANDHATRED #LIMBAS #ZADS ZAFAFA BIYAR KALBIM 500 mamuhgee A DUNIYATA 500 Huguma AJIYA A DUHU 500 Billyn Abdul KIRJIN ME HANKALI 500 Miss xoxo Pay at 0022419171 AccessBank Maryam sani gummi Shedan biya 09033181070 Or mtn vtu at 09032345899*_Arewabooks@Mamuhgee_* 38 *KALPANAH COLLECTION* 08105064494 Shin ke daliba ce ko kuma uwa wadda har yanzu bata daina rokon urgent 2k a wurin yan uwa da kawaye ba,tou nesa tazo kusa domin kuwa na kawo miki maganin matsalarki,domin kuwa *Kalphanah Collection* ta shirya tsaf domin taimaka wa duk wani dan kasuwa ko kuma wanda yake son fara kasuwanci.A *Kalphanah Collection* muna saida kaya kama daga Jaka,Takalmi,Atamfa,Laces,Kayan yara da kuma kayan kitchen.Wani abun mamakin ma muna saida kayan mu ga masu siyen daya ko kuma sari,ga waenda basuda jari ma mun tanadar masu hanyoyi daban daban da zasu fara neman na kansu.Hajiya kina gida kwace zaki dinga jin saukar kudi a asusun bankin ki.Ga musu fuskantar qalubale a kasuwancin su kuma an kawo muku sauqi domin kuwa an bude muku group dinku da zaku dinga tattauna matsalolin ku. https://chat.whatsapp.com/JMSe2The4Q2F5tLdzGduyC Kedai idan kin shirya ki dannan link din nan na kasa domin shiga group dinmu ki ganewa idonki kunsan ance gani ya kore JI Karki yadda ki wuce bakiyi joining group din nan ba domin kuwa yanzu sallah tana qaratowa ko bakiyi kasuwanci ba zaki siya domin amfanin ki na yau da kullun kuma ko baku buqata yanzu nan gaba zaku iya neman ta. Siyen na gari maida kudi gida. 08105064494 ********* Koda ya shige bayan yayi shirin bacci cikin kayan bacci masu santsi zaunawa yayi yana lumshe idanuwansa Sanyin Ac na ratsasa ahankali sbd babu alamar bacci a tareda dashi tinani me zurfi da mutuwar jiki ya rufesa duk da bazai taba sakin kari ba akan ciwon nata zaiyi yawon duniya ya nema mata lafia sedai idan Allah yayi itama barinsa zatai tukuna amma yana roko da fatar Allah yasa ya fara barin duniya idan har Ciwon nan mai dauketa ne daga duniyar karta barsa.. Sayd kuwa saida yasha magani me karfin gaske kafin gaske kafin bacci ya iya daukansa. Da asuba bayan sunyi sallah kowa ya koma bacci Guraren 8 na safe wayar Sayd ta tadasa bacci kansa da yayi masa nauyi sosai sbd maganin daya sha ya daga yana bude idanuwansa daqyar ya kai hannu ya dauki wayar yana dorawa a kunnensa. Fahad ne cikin girmmawa yace "Goodmorning Boss, Duka bayanan daka nema an hada na turo maka ka duba hotinansu da bayanansu tareda sunayensu suna nan" "Ok,thanks zan duba yanzun nan,i will get back to you akan sauran bayanin" Ok boss" Kashe wayar yayi yana komawa bacci sbd koya duba babu abinda zai gane yanzu dan maganin dayasha bai sakasa ba ko kadan. ***********Ahankali ta tashi daga kwancen datake idanuwanta biyu ba bacci take ba ta jima da farkawa kawai tashin ne ta kasa sbd a macen da jikinta yake da tinanin fuskan data kasa gogewa daga idanuwanta, Tinda ta dawo Nigeria ta rasa gane kanta da abinda ya maqale mata a tinani da ido wanda take ganin Shedan ne hakama tsananin ciwo da zafin hakan takeji sbd zuciyarta kwata kwata bata yadda tayi tinanin kowane namijin ba bayan Ammar Zad. Numfashi me sanyi ta sauke ahankali tareda lumshe fararen idanuwanta ta budesu tana daukan wayarta ta qurawa hoton Ammar dayake gaban wayarta ido tareda Ambatar sunansa ahankali tace "Ammar zad kai kadaine wanda zuciyar Jannah Zad ke so, Kaine mijina,kaine farin ciki na,kaine abinda kawai nake buqata zuciyata ta kammala" Rufe idanuwanta tayi ta bude tana ajiye wayar tareda ziro kafafunta qasa tana miqewa tsaye sanye da kayan bacci riga da wando masu kauri ta nufi toilet tana dafe zuciyarta dake bugawa ahankali tana jin kaman kalamanta ba daga zuciyar taya suka fito ba iya bakinta ne. Numfashi me qarfi ta sauke tana qarasa shigewa toilet din dan fitar da tinanin komai a zuciyarta. Brush tayi tana kallan fuskanta a jikin mirror wanda tayi fayau sbd tashinta kenan. Tana gamawa zare kayan jikinta tayi tana qarasawa bathtub ta kunna ruwan dumi ta shige. Ta jima kafin ta fito daure da blue towel ta nufi wayarta dake ringing ta duba taga sunan MAN dinta ne dan haka ta dauka tana zaunawa gaban mirror da wata muryan data sakasa ajiye Ipad din datake hannunsa yana duba sako ya ajiye akan table dayake gabansa na bedroom dinsa yana jinginar da bayansa muryan na kashe kowane irin kuzarin jikinsa da zuciyarsa yace "How are you Love?? Kin tashi? Numfashi me sanyi ta sauke tana kallan fuskanta tace "Goodmorning Love, Na tashi ina shiryawa am coming out for breakfast" "Ok take your time and kinsha maganinki kuwa? "Yes love" tafada tana kallan drawer din da maganinta suke ciki. Aje wayar sukai yana cewa ta kula gurin shiryawa kada ta wahalar da kanta. Shiryawa ta fara yi a natse tana gamawa ta saka free skirt da riga na Dior da scarf ta ziro flat versace ta fito riqe da wayarta wani lafiyayyan qamshi na tashi a jikinta na woodyLeather. Kai tsaye palon Dad ta nufa wanda yake palon zaune yana waya cikin nutsuwa da kwanciyar hankali tareda manyanci da Duniya data gama tsaya masa. Yana ganinta ya bude mata hannunsa daya ta qaraso ta zauna kusa dashi tana rungume hannunsa a jikinta ta bude baki cikin tsananin kaunarsa da sakewan datake tsakaninsu duka familyn tace "Goodmorning BestDad" (hakan itama take kiransa tin tana qaramarta) Murmushin farin cikin ganinta kafai da yayi ya fara sakewa kafin ya kashe wayar dayake yace "Morning My Angel, Kin tashi lafiya? Yaya maganinki kinsha kuwa? "Nasha kaima kasha naka Bdad? Amsawa yayi da cewa yasha yana murmushin jin dadi.. Shigowan Mimi ne ya sakata sake lafewa gefensa tana murmushi tace "Goodmorning Mimi, Kin tashi lfy? Qarasowa tayi tana zaunawa gefen dad din tace "Lfy kalau,kinsha maganinki? Yes" tace sbd tasan kowa a familyn babu ranar da babu wanda baya tambayar tasha maganinta. Ko gama magana da Mimi bataiba qamshin Ammar yafara shiga hancinta ta dago idanuwanta ta zubawa kofar sai gashi ya sako kai cikin wani irin class da nutsuwa sanyeda Ash balmains. Maheer ne shima ya sako kai tareda Anny tana gafensa kowannensu yana fidda nasa kalan qamshin na shegun designer Turaren dasuke amfani dasu masu tsadan gaske. Akan Ammar idanuwanta suke tana jifansa da kallan daya sakasa zuba mata nasa idanuwan yana jin idan da ya rasata a bayan da yanzu baya duniyar dan wlh bazai iya rayuwa babuta, Wani irin masifaffen sonta ne Allah ya halitta masa a zuciya da kirjinsa da ko tinanin rasata kadai idan yayi yake qarewa a hannun therapist dinsa sbd zarewa yakeyi gaba daya da iya wannan tunanin dan hakanne yasa yariga yasan babu rashinta a kundinsa saidai idan karshen tasa rayuwar ne yazo dan hakan ne bai taba jin komaiba a rayukan da suka hallakar dan nema mata zuciyar datake bugawa a kirjinta hakama da yau zaa ce wannan dinma ta gaza to tabbas zai koma farautan zuciyoyin mutane matacci da rayayyu dan nema mata lafiya kawai. Gefen Miminsa ya qarasa ya zauna yana kallan dad da murmushi da farin ciki a fuskansa yace "Goodmorning Dad" Amsawa dad yayi yana amsa gaisuwan Maheer shima kafin ta Anny wadda itama ta zauna gefen mijinta. Saleem ne ya shigo karshe yana waya fuskansa gabaki daya ba walwala. Kallansa sukai ganin yanayinsa ya saka yana gama wayar Maheer ya kallesa yace "Issue din Approval na wanda kakeson ne ko yaya?? Wayarsa ga ajiye gefensa yana sauke numfashi me zafin gaske yace "Yes,sunata rejecting din proposal dina batareda ma an tsaya andubaba" Da mamaki gabaki dayansu suka kallesa sbd jin wai rejection ga ZAADENs. Cikin rashin Bawa zancen mahimmanci sbd yasan bama abu bane me yiyuwa rejecting zaadens dad ya kalli Maheer yace "Handle the situation,koma waye ka tabbatar masa da yasan Zaadens ne zasuyi masa alfarma" Maheer saleem din ya kalla shima cikin hana ransa baci sbd baya buqatan sakawa kansa ciwo akan mutanen da basuda mahimmanci a taqaice yace "Wats the name??? "LIMBAs EMwrld" Ammar ne ya dago ahankali ya kalli saleem din hakama Dad da shi kansa Maheer din sbd sun san Kamfanin A suna sbd kusan duka abokan businesses nasu suna Yi dashi sosai hakama yana cikin masu kudin dasuke gogawa dasu duk da basu taba sanin junaba amma sunsan sunan hakama shima dole yasan sunansu. "AZIZ AY LIMBA the lucky Monster" Maheer ya fada yana kallan Saleem din. Yes" ya fada yana jin daci sbd LIMBAn kadaine wanda zai basu abinda sukeso a sabon business din nasu wanda yanaqi dole sedai suyi da qananun kamfani wanda ba girmasu bane hakama ci bayane garesu da kuma bazasu habbaku akaiba yanda sukeso. Ammar dayaji sunan Har cikin zuciyarsa kallan Maheer yayi yace "Banajin business dashi zaiyi amfani sbd yafara da zafin kai, Waye shi?" Ya tambaya yana kallan Saleem wanda ya dauki wayarsa daya ajiye gefensa ya nemo bayanin komai akan AY din dayake dashi sbd sosai yake bibiyarsa sbd shi ba qaramin aiki yakeson yayi a tareda Limban ba tamkar burine dayakeson cikawa na aiki dashi. Horonsa ne yana sanye da Fararen kaya da fcap zaune a kujera da qaramin table gefensa Asalin kyansa da kwarjininsa me tsanani a bayyane suke ko a hoton da alama gurin golf ne yake sbd kayan dayake jikiksa ya nuna hakan. Maheer kallo daya yayi masa ya karanto izzar data sakasa rejecting Zadeens dan haka ko bayanin komai bai tsaya karantawa ba yace da kansa zai gansa. Dad kuwa kallo daya yayi masa ya dauke kai sbd maheer zaiji da komai sedai yana hango zafin kai a tattarda da aura dinsa. Ammar ne ya zubawa AY din idanuwansa yana kallansa... Wani irin yanayi na qi da makamancinsa yaji yana shigarsa akansa, Dauke idanuwansa yayi akai yana sake qaramin tsokin inda AY din ya samu guts na rejecting dinsu. Jannah kuwa bisa ga rashin sani idanuwanta suka sauka akan fuskansa wani irin sanyi taji yana sauka jikinta tana zuba masa idanuwa zuciyar na harbawa ahankali cikin sanyi da nutsuwa. "AZIZ LIMBA" sunan ya sake shiga kanta ahankali tana sauke numfashi tareda dauke idanuwanta daga fuskansa tana maidawa kan Ammar ta zuba masa ido tana kalla jikinta na mutuwa. Jin idanuwansa akanta suna magana dasu dad ya sanyashi kallanta Murmushi me sanyi da kyau ta sakar masa tana bude bakinta batareda sautiba ta motsasu da cewa "My love" Murmushi ya sakar mata zuciyarsa na wankewa daga duka takaicin Limban daya cikesa. Basu fito breakfast ba sai bayan kusan mintina suka nufi dining room tana gefen Dad ammar na gefen Mimi Anny kuwa tana gefen mijinta tana tinanin inda ta taba ganin fuskan AZIZ AY LIMBA dinnan dasuka gani yanzu, Tabbas ta taba ganinsa ko wani me kama dashi duk da kamannin suna bace mata amma dai tasan ta taba gani sedai kuma ta manta kokuma kila shi dinne ta taba ganin hotonsa a media ko tv. Makeken dining me kujeru da yawa an cikesa da abinci kusan kala hudu sbd kowa da abinda yafi buqatan breakfast dashi. Maheer sun rigasa zama sbd saida yayi waya da PA dinsa akan yanason bayanin komai akan AZIZ AY LIMBA kuma yana son shi da shi su hadu akan business din Zadeens. Angama yace masa yana fara abinda aka sakasa, Shi kuma Maheer wayar ya kashe yana zaunawa dining sbd tabbas yanason haduwa da AZIZ LIMBA sbd yaga iya power din dayake dashi dan su sune power din da kansu. ************ Sayd sai karfe goma da mintina ya farka daga baccinsa kansa yayi masa tsananin nauyi ya bude idanuwansa yana tashi zaune kansa na sake masa nauyi sosai. Time ya kalla ya sauke ajiyar zuciya tareda miqa hannunsa ya dauki wayarsa yaga misscalls da yawa dan haka ya miqe da sauri duk da AY bazai fita aiki ba hutu yake amma shi akwai abubuwa da yawa dazai handling ciki harda top qwararrun cardiologist da aka hado zai gabatarwa AZIZ din. Ipad dinsa ya dauka dan duba sakon da Fahad ya turo akan binciken.. Kunnawa yayi tareda shiga sakon kai tsaye.. Hoton DR ABRAHAM SMITH ne abu na farko daya fara bayyana akan screen din tareda sunansa da manyan baqi tareda bayaninsa da qwarewansa......... Kansa da bai gama warwarewa bane yaji yayi masa dum kafafunsa suka kasa daukansa ya zube qasa a gurfane yana riqe ipad din datake kokarin subuce masa yana qura idanuwansa da suka bude gaba daya baccin cikinsu na fita sbd Shin babban Likitan da yayi aikin Ummitah dan bazai manta fuskansa ba abada dashi da sauran likitocin biyu daya dr Nicolas dayan dr ismail..... Rawa hannuwansa suka fara yana kasa riqe Ipad din ya lalubo wayarsa ya saka kiran Fahad. Yana dauka ya jefa masa tambayar "DR ABRAHAM SMITH likitan zuciya ne kokuwa gynecologist????? "Babban likitan Zuciya ne kuma kwararre shine top a list dinmu, Yayi aiki a Nigeria tsawon lokaci kafin ya koma Greece,bai taba zama gynecologist ba akwai dansa Dr Nico yana cikin list din shima cardiologist ne kwararre so...... Datse wayar Sayd yayi wayar na subuce masa daga hannu kansa na juyawa hakama zuciyarsa bugawa takeyi kaman zata faso kirjinsa ta fito...... Fuskan Dr Abraham ya qurawa idanuwansa da ganinsu ke ragewa yana fara ganin dishi dishi harya dena ganin komai ya zube a gurin. #MAMUH #THE ZAADENS #THE LIMBA #BILLIONAIRESWAR/REVENGE #CRAZYLOVE #HEARTACHE #AZIZ LIMBA #JANNAH ZAD #AMMAR ZAD #FALAQ #LOVE AND HATRED ZAFAFA BIYAR KALBIM 500 mamuhgee A DUNIYATA 500 Huguma AJIYA A DUHU 500 Billyn Abdul KIRJIN ME HANKALI 500 Miss xoxo Pay at 0022419171 AccessBank Maryam sani gummi Shedan biya 09033181070 Or mtn vtu at 09032345899*_Arewabooks@Mamuhgee_* 39 *KALPANAH COLLECTION* 08105064494 Shin ke daliba ce ko kuma uwa wadda har yanzu bata daina rokon urgent 2k a wurin yan uwa da kawaye ba,tou nesa tazo kusa domin kuwa na kawo miki maganin matsalarki,domin kuwa *Kalphanah Collection* ta shirya tsaf domin taimaka wa duk wani dan kasuwa ko kuma wanda yake son fara kasuwanci.A *Kalphanah Collection* muna saida kaya kama daga Jaka,Takalmi,Atamfa,Laces,Kayan yara da kuma kayan kitchen.Wani abun mamakin ma muna saida kayan mu ga masu siyen daya ko kuma sari,ga waenda basuda jari ma mun tanadar masu hanyoyi daban daban da zasu fara neman na kansu.Hajiya kina gida kwace zaki dinga jin saukar kudi a asusun bankin ki.Ga musu fuskantar qalubale a kasuwancin su kuma an kawo muku sauqi domin kuwa an bude muku group dinku da zaku dinga tattauna matsalolin ku. https://chat.whatsapp.com/IyDlSVdw1rDIlCNNQMel68 Kedai idan kin shirya ki dannan link din nan na kasa domin shiga group dinmu ki ganewa idonki kunsan ance gani ya kore JI Karki yadda ki wuce bakiyi joining group din nan ba domin kuwa yanzu sallah tana qaratowa ko bakiyi kasuwanci ba zaki siya domin amfanin ki na yau da kullun kuma ko baku buqata yanzu nan gaba zaku iya neman ta. Siyen na gari maida kudi gida. 08105064494 *************** Neman toshewa kirjinsa yakeyi yana jin numfashinsa na neman yankewa idanuwansa sukai jajir ya daga hannunsa daqyar baya gani sosai ya kamo wayarsa dake yashe a qasa ya saka kiran fahad sedai kafin fahad din ya dauka numfashinsa ya sarke a gurin. Fahad na dauka cikin girmmawa ya fara magana yaji shiru. Cire wayar yayi daga kunnensa ya duba yaga kiran na tafiya ya sake dorawa kan kunnensa yana ambatar sunansa da girmamawa. Jin shiru saiya kashe ya saka kiransa tafara ringing harta katse baa dagaba Sake saka kiran yayi yana kallan time kafin ya juya kan motarsa kawai zuwa LIMBAs din batareda ya dena kiran wayar ba. Koda ya iso Babu wanda ya fito gidan tsit hakama baa zuwa bangaren AY sbd a ciki yake sosai bare yaje yafara kai masa gaisuwa dan haka Fiddausi da masu aiki ne sukai masa barka da zuwa dayake shima kowa a gidan ya sansa tinda duka yaran Limban ne. Amsawa kawai yayi ya nufi bangaren Sayd yana isa so daya yayi knocking kafin ya bude kofar bedroom din nasa. Abinda ransa ya basa na cewan ba lafiya ba ne yaci karo dashi sbd a kwance Sayd din yake a qasa yana kokarin samun attack sbd numfashinsa dake kokarin yankewa sbd shock. Da saurin gaske Fahad yayi kansa yana ambatar sunansa tareda basa taimakon gaggawa sbd kada numfashin nasa ya yanke sedai kaman hakan bazaiyiba dan haka da sauri ya kamasa ya maidasa kan lafiyayyan gadonsa dake dakin ya daga wayarsa da sauri yana kiran dr. Yana samun likita da sauri ya sanar dashi suna buqatan taimakon gaggawa a gidan. Yana kashe wayar kansa ya koma yana kokarin taimaka masa gurin saisaituwan numfashin yana miqewa da sauri ya dauko abu yana fifita masa sbd ya samu iskan shaqar sbd kamanma suffocating yake. Andauki mintina sosai kafin dr Raheem ya iso gidan wanda zuwansa ne yasa mutan gidan suka san abinda yake faruwa dan haka cikin tashin hankali mama da Fiddausi sukayo dakin bayan maman ta kira wayar AZIZ ta sanar dashi Sayd ba lafiya. Kansa dr Raheem yayi da sauri yana kallansa yasan attack ne ya samu... AZIZ dinne shima ya iso dakin a natse babu walwala a fuskansa Kallansa mama tayi cikin kulawa da damuwa tace "Kaima kaman bakada lafiyar AZIZ, Lafiya kuwa? Jamaa meyake faruwa? Baice komaiba ya nufi Sayd din wanda Dr Raheem ke dubawa yana ambatar sunansa cikeda kulawa. Gefe Fahad ya matsa cikeda girmamawa yana masa barka da fitowa. Amsawa yayi yana kallan Sayd din ya jefawa Fahad tambayar "Me faru? Meya samesa?" Dagowa Fahad yayi yana kasa kallan AZIZ din dika yace "Bansaniba,mungama waya dashi akan reports da profiles na Doctors da aka buqata ne dana turo masa, Sai kuma daga baya ya sake kira ya tambayeni qarin bayani akan daya daga cikinsu na fada masa abinda na sani akai wanda it seems like ya sansa kokuma makamancin hakan sai kuka gashi ya sake kirana banaji koda na iso na samesa ya samu attack so i called Dr Raheem" Shiru AZIZ din yai yana sake maida idanuwansa akan Sayd da idanuwansa sukai jajir numfashinsa ya fara daidaituwa sedai yaqi dago kansa ya kalli AZIZ din wanda yake nazartan yanayinsa sbd kaf duniya a yanzu bayajin akwai abinda zai saka Sayd din samun attack yanda zuciyarsa ta kangare ya zama wani irin me tsananin karfin hali dan haka koma menene akwai abinda ya sakasa samun attack din lokaci daya. Kan Dr Raheem ya maida idanuwansa dake juyawa ahankali ya bude baki a natse yace "Yaya?All good,right Dr? Juyowa Dr Yayi ya kalli AZIZ din yana dan sauke numfashi yace "Yes attack ne due to shock kawai ba komaiba amma yanzu insha Allah zai daidaita tinda numfashinsa ya dawo daidai" Numfashi me sanyi da nutsuwa ya sauke yana kallan Sayd din yace "Ka kashe wayoyinka ka huta dakyau coz lafiyanka na gaban komai ka kula,Allah ya tsare gaba" Gyada kai sayd yayi yana kasa dagowa sbd sam baya iya ko hada ido da AZIZ din sbd tsoro ma yakejin yana rufesa da wata irin tashin hankali na fargaban abinda zai iya biyowa baya idan abinda yake gani yana shirin zama gaskia Juyawa sukai kowa ya fice daga dakin dan barinsa ya huta ko zai sake warwarewa. Fahad kadai aka bari wanda Sayd ya dago jajayen idanuwansa ya kalla yana sauke wani nannauyan numfashi mara karfi sbd karfinsa da yayi kasa sbd attack din. Fahad ma kallansa yayi cikin kulawa yana sake masa sannu ya tattara ipad dij sayd din da qasu abubuwan da suka zube ya sauke ya dauka a table dayake tsakiyar dakin yana kallan time yace zai tafi yaji da office tinda yau daga shi har Ogan kwata kwata bame shiga office din. Cikin nauyin muryansa datai kauri sosai sbd nauyin dayakeji a kirjinsa na tsoro da tashin hankali tareda wani irin masifaffen tiriri da zafi ya bude baki yakira Fahad din. Dakatawa yayi tareda juyowa yana dawowa cikin girmmawa ya bude baki zaiyi magana Sayd ya katsesa da cewa "Dr Abraham a wane asibiti yai aiki a Nigeria?? Ipad dinsa ya koma motarsa ya dauko ya dawo yana bude duka bayanan daya samu akansa na fili dana boye ya fara karanto masa "ZAADEN HLTH CEN/SPEACIALIST, Yayi aiki tareda Dansa kaman yanda na fada maka, Yanada kusanci da ZAADENs sosai coz sun zama tamkar family" Shiru Sayd yayi yana shiga tinani kafin ya sake bude baki yace "Alaqar menene a tsakaninsa dasu da suka samu kusanci? I mean wane hulda ne tsakaninsu? Is he a business man apart from being a Doc??" "Nope" fahad ya fada yana sake duba profile din Dr Abraham din dakyau wanda aka hada aka turo masa. Dagowa Sayd yayi ya kalli fahad yana sake shiga tinanin dayake nauyaya kansa ya bude baki yace "Shine family doctor na ZAADENs kenan? Yes" "Meya hadasu da likitan zuciya da iya aikin zuciyar ya sani dazai zama family doc dinsu wanda har suka taho dashi qasarsu? "I don't know that Boss Amma akwai yiyuwar sunada patient me heart problem din shiyasa ya zama family but..... Katsesa Sayd yayi cikin Wani irin sautin daya saka fahad din kallansa da sauri.. "Inason full background details na ZAADENs tin daga Kakansu asalin Zad din har zuwa yanzu, Inason medical history da health status dinsu da komai, Idan nace komai ina nufin har wanda bai kamata a saniba inason full dets, Ko nawa zaa kashe ina son samun wannan bayanin komai kada a bari kota yaya koda hakan na nufin kidnapping wani ne i mst get the dets" Shiru Fahad yayi sedai kuma yasan komai zaiyi saiyayi ya samo bayanan da Sayd din ya fada sbd AZIZ LIMBA idan yace yanason details to yana nufin yana sonsu by all means dan haka tinda ya fara aiki dasu babu wani details na sirri da wanda bana sirrinba da baya iya bi ya binciko sbd Allah ya basa wata irin naci da baiwan iya bin sirri ya nemota. "Yes boss insha Allah zan hada duka bayanan" Gyada kai sayd yayi yana rufe idanuwansa sbd nauyin da kansa keyi sbd tinanin dayake sake rikita kansa. Fitowa fahad yayi yana daga wayarsa dan kira yafara bincikensa ayau din duk da ayyukan sun masa yawa ga office ma ana jiransa. Harabar gida ya fito yana nufar motarsa bayan ya kashe wayar dayayi yana kokarin bude motar sako ya shigo wayarsa. Saida ya shiga motar ya zauna zai tada motar yaga sunan SIR LIMBA ne ya turo sakon. Saurin bude dakon yayi yana karanta layi daya daya rubuto masa. "In my office" Kashe wayar yayi ya bude motar yana fitowa dauke da ipad dinsa da wayarsa sbd yasan aikine so dole kila akwai yiyuwar buqatar ipad din tinda komai na ayyukansu da ita sukeyi. Office dinsa na cikin gidan ya nufa yana dan daidaita nutsuwarsa. Knocking yayi a natse so daya kafin ya bude kofar office din wadda qamshin AZIZ dinne ya fara kado masa cikin sanyi da nutsuwa, Yana zaune akan sofa ta hutawa dake office din wayarsa na kan table din gabansa fuskansa fresh ba yanayin komai akanta sai aura dinsa data cike gurin ba hayaniya. Qarasowa fahad yayi yana dan kallan AZIZ din cikin girmmawa da tsananin kaunarsa dayake. Cikin girmmawa yace "Gani" Idanuwansa ya dago ya kalli fahad din dasu ya sake dan karantar yanayinsa kafin ya bude baki yace "Meyake faruwa? Wane doc ne Sayd yake neman qarin bayani akansa? Ipad dinsa ya dago ya nemo profile din Dr Abraham da komai daya hada yake ciki ya qaraso gaban AY din ya basa cikeda girmama yana cewa "Dr Abraham,daya daga cikin manyan kwararrun likitocin Zuciya da muka binciko sbd Matsalar Falaq Aziz, Yayi aiki a Nigeria dan lokaci kafin ya baro, Close family friend ne na ZAADENs wanda kuma a Nigeria dinma a asibitinsu yayi aiki, A yanzu cikakkiyar bincike da bayanin asalin alaqar data tsakaninsa da ZAADENs Sir Sayd yace a binciko masa,sai kuma idan ya taba zama gynecology doc wanda kuma tin a gurin binciken namu babu inda ya taba zama gynecologist........ Dagowa AZIZ yayi da fararen idanuwansa daya zubawa Dr Abraham din ya kalli Fahad a natse yace "Gynecology Doc?? Meyasa yake son sanin hakan? "I don't know Sir but yanason sanin Medical history na familyn zadeens gaba daya wanda inaga kaman yana tinanin akwai me ciwon zuciya a cikin familyn shiyasa suke tareda dr Abraham din kuma ya dage yanason sanin Meya hada likitan zuciya dana mata" Shiru AZIZ yayi yana sauraron bayanan suna shiga kansa daki daki yana tinani akansu sbd sanin Sayd baya binciken abinda baida tsananin mahimmanci hakama tareda boye masa wanda hakan ne ya saka tinaninsa tsayuwa akan koma menene yanason confirming nasa ne kafin fada masa, Idan har sai yayi confirming kafin ya sanar dashi to tabbas mahimmancin abin na tattareda hadarin dayake gudin basa false bayani... Shiru gurin ya sake dauka kafin Wayarsa dake gabansa ya miqa hannunsa ya dauka batareda yace komaiba ya nemo Numbern Alh Saad ya saka kira kai tsaye. Ringing uku tayi aka dauki wayar Cikin kwanciyar hankali a natse suka gaisa tareda tambayar su Falaq dasu mama yace duk suna lafiya shima ya tambaya su anty maryam da sauran yaransa da suka zama yan mata duk suna university. Kai tsaye bayan gaisuwar ya jefa masa tambayar data saka Alh Saad din Ajiye cup Tea dayake hannunsa yana sha a natse cikim lafiyayyan palonsa dayake katafen gidansa. "Wane Asibiti ne Ummitah ta haihu???" "ZAADEN" Alh Saad ya fada cikin tsananin mamakin tambayar sbd tinda akai rasuwar yayi jinya ya warke har yau bai taba tambaya ko fadar magana ko daya akan ciwon datai da rasuwarba shiyasa suma sukai shiru babu wanda ya fada masa irin yanda taita jinya kafin haihuwar sbd ya zabi danne ciwon rashinta a ransa ya mutu dashi batareda yaji azabar ciwon datasha ba wanda zai qarasa dagargaza karfin zuciyar daya sakawa kansa ne. #MAMUH ZAFAFA BIYAR KALBIM 500 mamuhgee A DUNIYATA 500 Huguma AJIYA A DUHU 500 Billyn Abdul KIRJIN ME HANKALI 500 Miss xoxo Pay at 0022419171 AccessBank Maryam sani gummi Shedan biya 09033181070 Or mtn vtu at 09032345899*_Arewabooks@Mamuhgee_* 40 *KALPANAH COLLECTION* 08105064494 Shin ke daliba ce ko kuma uwa wadda har yanzu bata daina rokon urgent 2k a wurin yan uwa da kawaye ba,tou nesa tazo kusa domin kuwa na kawo miki maganin matsalarki,domin kuwa *Kalphanah Collection* ta shirya tsaf domin taimaka wa duk wani dan kasuwa ko kuma wanda yake son fara kasuwanci.A *Kalphanah Collection* muna saida kaya kama daga Jaka,Takalmi,Atamfa,Laces,Kayan yara da kuma kayan kitchen.Wani abun mamakin ma muna saida kayan mu ga masu siyen daya ko kuma sari,ga waenda basuda jari ma mun tanadar masu hanyoyi daban daban da zasu fara neman na kansu.Hajiya kina gida kwace zaki dinga jin saukar kudi a asusun bankin ki.Ga musu fuskantar qalubale a kasuwancin su kuma an kawo muku sauqi domin kuwa an bude muku group dinku da zaku dinga tattauna matsalolin ku. https://chat.whatsapp.com/IyDlSVdw1rDIlCNNQMel68 Kedai idan kin shirya ki dannan link din nan na kasa domin shiga group dinmu ki ganewa idonki kunsan ance gani ya kore JI Karki yadda ki wuce bakiyi joining group din nan ba domin kuwa yanzu sallah tana qaratowa ko bakiyi kasuwanci ba zaki siya domin amfanin ki na yau da kullun kuma ko baku buqata yanzu nan gaba zaku iya neman ta. Siyen na gari maida kudi gida. 08105064494 ************** "Thank you" AZIZ yace yana kashe wayarsa ya ajiye gefensa ya dago ya kalli fahad dayake jiran umarninsa bude baki yace "Dukkanin Abinda ka sani na bayanin daya buqata ka hadosa cikin gaggawa inason sanin koma menene daya shafi wannan maganar" Cikin tabbatarwa Fahad yace "Angama Sir" Harya juya zai fice AZIZ din ya kirasa ahankali yana juyowa yace masa yanason Ipad din Sayd a hannunsa yanzu. Ficewa fahad yayi ya koma dakin Sayd wanda yake toilet yana sakarwa kansa ruwan dumi sbd sake samun karfi. Baima tsaya komaiba daukanta kawai yayi ya fice ya kaiwa AZIZ wanda yana karba mai tsaye history na browsers dinsa ya ringa shiga. Shiru yayi yana bin duka histories din wainda duka bincike ne kawai yake akan Masu ciki da yanda ake cire zuciyar dan adam sai kuma bincike akan scar din da aikin zuciya yake bari wanda kusan shine yafi yawa. Shiru yayi yana ajiye ipad din gefensa tareda dan rufe idanuwansa yana hana kansa tinanin komai dan baisan me sayd zaiyi da wannan binciken ba seda kuma binciken da zaayi akan zaadens ne yake buqatan sanin dalili ga kuma dr Abraham da shima yake nacin neman bayanin komai akansa wanda duka idan aka hada link daya ne asibiti tinda shima Sayd idan har yasan Abraham a asibitin ne wanda duka kuma dai haihuwan Ummitah ce takaisu asibitin da har akai haduwar. Nunfashi mara sauti ya sauke yan bude idanuwansa ya dauki wayarsa ya miqe yabar office din zuwa cikin gida. Kai tsaye dakin Sayd din ya sake zuwa ya dubasa ya tararda ya kwanta bacci ma ya daukesa dan haka ya wuce nasa bangaren bayan ya sanarwa mama ta kwantar da hankalinta b damuwar komai bane may be ma stress ne na aiki da zaman da basu cika yiba. Yadda mama tayi ta dan kwantar da hankalinta sbd Sayd shima 'da ne gareta tana kaunarsa sosai da sosai. Falaq bata gida tana school shiyasa gidan yake tsit sai data dawo hayaniyar gidan ta dawo. Abincin rana gabaki dayansu gidan sukaci a dining kaman yanda suka saba Sayd ma ya fito dashi akaci abincin sbd bayason yabar kofar da AZIZ zaisan akwai abinda bayason ya sani dan haka ya sake. AZIZ din kuwa ganin ya sake batareda ya sanar dashi komaiba ya sakasa tabbatarda abinda yake binciken ba alkhairi bane tinda yake kokarin boye masa. Da daddare da kansa ya raka Falaq dakinta sai datai bacci ya fito ya wuce bedroom dinsa yana kashe wayoyinsa, Wanka kawai yai yayi shirin bacci ya kwanta yana rufe idanuwansa batareda bacci yazo masa ba sbd abubuwa da yawa ne a zuciyarsa da kansa wanda duk dare kafin ya kwanta kewar yar uwarsa ce take zuwar masa wadda yakewa fata da adduar tana cikin rahamar ubangiji. **Washe gari ma basu fita aiki ba a gida suka wuni Sayd din ya sake warwarewa shima kuma hutu da kadaici yake so dan haka ko fitowa baiyiba abincinsa ma sedai aka kai masa palonsa aka jera masa acan yaci. Sayd kuwa Fita yayi sbd tsananta bincikensa da ayanzu shine abinda yake tsananin buqata. Wayar Latif Sayd ya kira wanda yake cikin yan Amanar maaikatan AZIZ kuma duk da basa kasar haryanzu LIMBA na biyansa Albashi hakama shine drivern da duk yawon asibitin da sukai harma da ranar haihuwa shine yake yawo dasu har suka baro Nigeria shine drivernsu. Latif dayake Shagonsa daya bude yana business dinsa yana ganin kiran ya daga cikeda girmamawa yana cewa "Oga Sayd" Gaisawa sukai Sayd din ya gyara zamansa yana sauke numfashi me sanyi kafin ya bude baki cikin bayyanarda Buqatan abinda zai tambaya batareda delay ba Shima Latif din Nutsuwa yayi yana aje abinda yake tareda wucewa kurya inda baa shiga saishi kadai ya zauna dan jin abinda Sayd din zai fada. "Latif ka tina a ranar da Ummitah ta rasu akwai Dr da shine yayi mana bayani kuma shine ya kula damu a wannan lokacin??? Cikin nazari Latif ya dan shiga tinani yana kokarin tinawa da lokacin sbd dashi suke tare a asibitin. Cikin rashin tabbatarwa yace "Eh wani black haka naji suna kiransa da kaman Dr samail ne ko yaya ma suna.....katsesa Sayd yayi da sauri da cewa "Yes,yes yes Dr Ismail,yes thats the name" Jin yayi wani abu daya danne zuciyarsa ya dan fada ya sauke numfashi yana miqewa tsaye yana jin sassauci a ransa yace "Latif inason kaje asibitin ka bincikamun Dr Ismail din, Inason sanin bayanai akansa, Waye shi, Familynsa, Aikinsa, Yana ina yanzu? Da address dinsa, No i want to know every single abu akan rayuwarsa cikin gaggawa" Shiru Latif yayi kafin ya sauke numfashi yace "Angama Oga Sayd sbd babu abinda bazan iya yiwa Familyn Sir AZIZ ba, Ayau zan ziyarci asibitin na fara sanin Full name nasa da idan yana nan kafin sauran binciken zuwa gobe da kwana biyu zan hado maka komai" "Thanks" sayd yace yana kashe wayarsa ya wurgar a kujera yana dafe kansa tareda lumshe idanuwansa. Falaq data kasa gane kan daddynta kwana biyu damuwa ta shiga tafara dagawasu mama hankali wadda itama tane kasa gane kan AZIZ din da kuma sayd da shima duk ya kasa zama kwana biyu Magana tai musu wanda ya saka Falaq dawo da Daddynta daidai shima sayd ganin AZIZ baice masa komaiba kuma yasan yanda AZIZ din yake da karantar abu da ilimin gane abu atake ya sakasa dawowa daidai sbd tsaro. ********cikin kwana biyu Fahad da Latif suka duqufa da mugun bincike da bin duk wata hanyar samo bayanan da suke nema baji ba gani, Shi kuma Sayd jin yake kaman zai zare sbd jiransu Amma ya boye yana ayyukansa hankali kwance sbd AZIZ daya fara fita office dan haka ya dan zama busy da ayyuka da kuma handling abubuwa. Latif ne yafara hada bincikensa dan haka ya kira Sayd din kai tsaye wanda a lokacinda kiran ya shigo yana gaban AZIZ LIMBA yana karanto masa bayanan Report da aka aiko musu daga Italy. Sunan Latif ne ya bayyana Akan screen din wayar Sayd din datake ajiye a gabansu. Hannu Sayd ya miqa ahankali ya dauki wayar tareda kashewa ya ajiye gefensa yana cigaba da bayanin da AZIZ ke sauraronsa hankali kwance cikin nutsuwa. Yana gama bayanansa juyawa yayi ya fice yana amsa wayar Pa din Maheer Zad data shigo wayarsa akan haduwarsu da haryanzu baa san lokacin ba.. Sayd na fita kai tsaye ya katse wayar dayake ya nufi office dinsa yana saka kiran Latif wanda ya dauka take. "Oga Sayd I've Send you every information daka buqata, Cikakken Sunansa Dr Ismail Saraki, Yana Nigeria haryanzu sedai yana jinya haka kawai aka wayi gari ya samu stroke baya iya magana baya iya komai yana gida yana jinya tareda familynsa a Jos, Likitan zuciya ne shima kuma bai taba aiki a kowane asibiti ba Nigeria sai zaaden sbd baa Nigeria din yake aikiba saida Zaadens suka basa babban matsayi a asibitinsu ya dawo Nigeria, Address da duka sauran bayanin na turo maka komai" Katsesa Sayd yayi da cewa "Idan yana aiki a Zaadens a babban matsayi meyasa basu tsaya masa gurin neman lafiyarsa ba ya koma gida?? "Ba shine abin tambayarba Abin mamakin shine Duk wani hanyoyin samunsa sun datse hakama komai ya rasa a qanqanin lokaci wanda kaman ana kokarin hanasa wani abun ne kokuma akwai abinda yayiwa Zaadens din nake ganin" Ajiyar zuciya Sayd ya sauke yana cewa "Ngd Latif zan sake nemanka sbd Zuwa jos zai kamaka" "Ok Thank you Oga Sayd" Yana kashe wayar ya miqe yana sauke ajiyar zuciya akai akai sbd komai ya fara fito masa sedai tsoron qarasa bincikawan yake ma dan abinda zai binciko kada ya kashe AZIZ. Sai yamma suka dawo gida suna isowa AZIZ kai tsaye bangarensa ya nufa yai wanka ya shiryo ya fito suka zauna cin abinci a dining falaq nata masa labarai kala kala wadda a duniya ita kadaice take ajiyesa tayita basa labarai da surutai kala kala ya bata kunnuwansa yana saurara batareda yace komaiba. Suna gamawa suka wuce sallah Saida sukai ishai suka dawo, Motarsu na shigowa harabar gidan motar Fahad na shigowa bayansu dan haka a tare sukai parking. Fahad dinne ya rigasu fitowa sanye cikin three quarter da farar sweatshirt ya nufo motarsu ya budewa AZIZ motar yana masa barka da dawowa. Amsawa yayi yana kallansa a taqaice ya nufu hanyar studyroom dinsa suka nufi bayansa. Yana shiga zaunawa yayi tareda ajiye wayarsa gefensa ya dago a natse ya kalli Sayd wanda yake kallan Fahad kafin ya maida kallansa kan Fahad din ya bude bakinsa yace "Yes,the dets??? Kallansa Sayd yayi da sauri yana matsowa zaiyi magana AZIZ din ya dago manyan fararen idanuwansa yai masa kallo daya take ta dakata yana komawa baya ya saukar da kansa zuciyarsa na tsananin nauyi da tashin hankalin abinda fahad ya samo akan binciken. Fahad da shima yake a natse sbd a gaban AZIZ din suke ipad dinsa ya daga ya fara budo bayanan yana cewa "Babu Alaqar kowane business dake tsakanin Zaadens da dr Abraham saina likitanci wanda kaman yanda muka zarga akwai me ciwon Zuciya a familyn sunanta ZEYNAB ZAD sedai kuma ta rasu da dadewa, Bayan rasuwarta Zadeens sun sake samun mace a familyn wadda duniya ta sheda yanda suke tsananin sonta amma kuma tana tsaka da karatu kawai aka nemeta aka rasa baa sake samun labarinta ba tsawon shekaru sun boyeta batareda an sake taba ganintaba wanda babu wanda yasan dalilin hakan amma kuma a yanzu tana wannan qasar tana karatu sedai ta koma gida a yanzu batanan, A familyn kowa mun samu bayanin cikakkiyar lafiyarsu banda JANNAH ZAD wadda babu wanda a iya binciken danai babu likitan daya taba ganinta bayan Dr Abraham......" Dan shiru yayi yana tinani da shakkar abinda zai fada kafin ya dago ya kalli sayd wanda shima shi yake kalla da dukkanin imaninsa kafin ya juyo ya saci kallan AZIZ da yayi shiru yana sauraronsa da dan sassauta murya yace "A yanda na tabbatar sbd bamu san health status din JANNAH ZAD ba a cikin familyn kuma dr Abraham ne kadai likitanta kuma Shi din likitan zuciya ne Tabbas itace takeda matsalan Zuciyar datake cikin zaadens, Dr Abraham ya samu zomowa babban likitan dayake cikin manyan doctors na duniya tareda tarin dukiya me yawan gaske daya zamo babba sbd zaadens da suka tsaya masa, Jannah Zad itace rai da Zad sukafi so fiyeda komai da suka mallaka a duniya... Dago idanuwansa yayi Ahankali ya saukesu akan Sayd sbd a duka bayanin baiji wani abin daya shafesu ba bayan maganar ciwon zuciyar datai kama data tasa 'yar dan haka ya zubawa sayd idanuwansa yana jiran bayaninsa wanda bayani kawai yakeso gamsashe batareda wani kwana ko daya ba. #MAMUH #BEST REVENGE #BEST LOVE #CRAZY LOVERS #SELFMADE BILLIONAIRE ZAFAFA BIYAR KALBIM 500 mamuhgee A DUNIYATA 500 Huguma AJIYA A DUHU 500 Billyn Abdul KIRJIN ME HANKALI 500 Miss xoxo Pay at 0022419171 AccessBank Maryam sani gummi Shedan biya 09033181070 Or mtn vtu at 09032345899*_Arewabooks@Mamuhgee_* 41 *KALPANAH COLLECTION* 08105064494 Shin ke daliba ce ko kuma uwa wadda har yanzu bata daina rokon urgent 2k a wurin yan uwa da kawaye ba,tou nesa tazo kusa domin kuwa na kawo miki maganin matsalarki,domin kuwa *Kalphanah Collection* ta shirya tsaf domin taimaka wa duk wani dan kasuwa ko kuma wanda yake son fara kasuwanci.A *Kalphanah Collection* muna saida kaya kama daga Jaka,Takalmi,Atamfa,Laces,Kayan yara da kuma kayan kitchen.Wani abun mamakin ma muna saida kayan mu ga masu siyen daya ko kuma sari,ga waenda basuda jari ma mun tanadar masu hanyoyi daban daban da zasu fara neman na kansu.Hajiya kina gida kwace zaki dinga jin saukar kudi a asusun bankin ki.Ga musu fuskantar qalubale a kasuwancin su kuma an kawo muku sauqi domin kuwa an bude muku group dinku da zaku dinga tattauna matsalolin ku. https://chat.whatsapp.com/IyDlSVdw1rDIlCNNQMel68 Kedai idan kin shirya ki dannan link din nan na kasa domin shiga group dinmu ki ganewa idonki kunsan ance gani ya kore JI Karki yadda ki wuce bakiyi joining group din nan ba domin kuwa yanzu sallah tana qaratowa ko bakiyi kasuwanci ba zaki siya domin amfanin ki na yau da kullun kuma ko baku buqata yanzu nan gaba zaku iya neman ta. Siyen na gari maida kudi gida. 08105064494 ************ Sayd daya cikin tsananin shock da mamaki da sauri ya karbi ipad din ya zubawa hoton Jannah idanuwansa wadda shekarunta suke kusan daya dana Ummitah.. Hannuwansa na rawa ya ciro wayarsa cikin jikinsa ya saka kiran Latif wanda a cikin bayaninsa yace masa a ranar da akai aikin Ummitah doctors din hudu ne ba uku ba kuma yaga dayan bayan ya fice daga gurin yana cire facemask kuma yaji nurse data biyo bayansa ta kirasa da Dr Zad sedai baiga fuskansa ba. Cikin sauri yacewa fahad "Turawa Latif hotunan familyn Zaadens gava dayansu yanzu" Daukan wayar Latif yayi take sayd yace masa "Duba ga sako nan fahad ya turo mata kaga idan akwai dr Zad din ranar haihuwan Ummitah" Kalman data saka AZIZ rufe idanuwansa kenan yana hadiye shirunsa gaba daya tareda wani irin ciwo da radadi suka gama shigewa cikinsa ya bude baki da fushi yace "Meyake faruwa nake tambaya anan" Bude baki Sayd yayi zaiyi magana Latif ya kira AZIZ yace ya ajiye wayar ya saka handsfree. Cikin tabbatarwa Latif yace "Tabbas naji an ambaci dr Zad amma wlh banga fuskanba sedai koma waye a cikinsu ne sbd su kadaine Zad" Kashe wayar sayd yayi yana jin kaman zai fasa wayar hannunsa sbd rashin samun tabbacin ganin fuskan. Cikin wani irin matsanancin ciwo da radadin zuciya ya dago ya kalli AZIZ AY LIMBA ya bude baki da tsananin rauni yace "A ranar da Ummitah ta rasu gurin wankanta akwai dinki a kirjinta setin zuciyarta sabo wanda a ranar ta samesa sbd koda muka kaita asibiti nine nai shirinta na tabbatarda babu wannan dinkin a kirjinta, A cikin likitocin da sukai mata aikin haihuwan babu gynecology doc ko daya a cikinsu, Babu aikin haihuwa a cikinta wanda shima na bincika idan har babu aiki a ciki to tabbas da kanta ta haihu ba aiki akai mata ba,to amma bayyanar aiki a kirjinta shine abinda nakeson sani, A asibitin zadeens akai mata a aikin, Likitocinsu ne, A familyn a akwai me ciwon zuciyar da bamu san waye ba, Meyesa suka dauki nauyin kai mata gawarta kyauta har gida? Meya hada haihuwanta da likitocin zuciya?????.......... Tsit gurin ya dauka sbd mutuwar tsayen da fahad yayi da fahimtar inda zancen ya dosa, AY din kuwa ajiyan zuciya ya sauke me sanyi kansa na kwakwalwansa na kasa daukan me Sayd din ke kokarin fada sbd bame yiyiwa bane har abada hakan sedai kuma baya wasa ko kadan da abinda aka ambaci sunan Ummitah a cikinsa koda kuwa bata raye dan haka ya kallesa a natse yace "Ina dayan dr din da kake maganar? "Yana jos" "A shirya tickets zamu kai masa ziyara lokaci yayi da zansan a hannun waye UMMITAH ta cika da time data rasu" ya fada kai tsaye yana miqewa yabar dakin kirjinsa na wani irin riqewa amma kuma lokaci yayi da fuskanci abinda yaketa gujewa shekara da shekaru musamman a yanzu da wannan unbelievable lamarin yake shigowa a lamarin. Sayd da babu abinda yakeso din kaman ya gansu a Nigeria din daman sbd ya fuskanci Dr ismail da kansa take ya kalli Fahad yace "Ayi clearing gaba daya appointments na AY din da schedules nasa na satin gaba daya har zuwa wani satin" Yes" fahad ya fada yana juyawa shima ya fice, Sayd din kuwa take ya kira ya saka akai musu booking ticket din tafiya ba bata lokaci. Mama batasan da tafiyarsu ba sai washe gari kawai kai tsaye taji tafiya AZIZ din zaiyi Nigeria da bayason zuwa tinda Ummitah ta rasu dan haka tasan koma menene zai kaisa yanada matiqar mahimmancin gaske wanda kilama ya shafi Ummitah ko falaq ne dan sune kadai zasu sakashi zuwa Nigeria lokaci daya. Cikin kwana biyu aka gama komai jirginsu ya saika Nigeria. A lagos suka sauka kuma anan zasu zauna dan bayajin zai iya zuwa abuja dan haka lafiyayyan Lodge ya sauka wanda securities dinsa kadai da tsaron gurin zakasan ko masu kudin sai wainda suke amfani da dollars ne ke suke gurin. Koda suka iso lagos din a daren shima latif jirginsa ya sauka a lagos daga abuja dan haka bai samu ganin AZIZ dinba sedai Sayd sai washe gari Sayd ya shiga dashi inda AZIZ din yake ya gaidasa cikeda farin cikin ganinsa da tsananin girmamawa da kaunar dayake masa. Abinda ya kawosu shi Sayd yake dan haka kwanansu daya a lagos ya nufi jos tareda Latif daman tin kafin su iso Nigeria Latif yaje jos din yayi confirming address din Dr ismail ya kuma gansa ya tabbatar da shi dinne dan haka koda suka isa jos lafiyayyan masauki su sauka sai washe gari suka isa gidansa inda suka tarar dashi zaune daure a kujera baya iya komai. Dayake ansan ana zuwa dubasa duk da ya dauki shekaru a hakan shiyasa kai tsaye suna fadar gurinsa suka taho dubasa aka shigo dasu har palonsa yana zaune abin tausayi kan kujera an dauresa da belt sbd fadowa dayake. Sayd ne a gaba sai Latif yana bayansa suka shigo da sallama.... Idanuwansa dake rufe ya bude ya saukar dasu akan Sayd wanda ya sauya gabaki daya sedai kuma kamanninsa basu sauya daga Idanuwansa ba sbd dasu yake kwana a ransa dasu yake tashi sbd sanadin komai da akai musu yake tamkar matacce yanzu rai ne kadai banbancinsa da matacce dan shima mutuwar yake fada tafi masa akan azabar dayake ciki. Wasu zafafan hawayene masu tafe da radadin dayake zuciyarsa da danasanin da batada amfani suka gangaro gefen Idanuwansa yana kasa kallan fuskan Sayd din wanda shi kuma hawayen dr ismail din da kallan daya kasa masa ya saka zuciyarsa fara karyewa dan abinda yake shirin tabbata... Zaunawa sukai suna mai masa sannu da fatan samun lafiya sedai kwata kwata Dr ismail din ya kasa kallan Sayd sai hawaye yake zubarwa. Shiru sukai babu wanda ya iya cewa komai saida matarsa ta shigo Sayd din ya kalleta yana mata tambayoyi akan yanayin jikin nasa tana masa bayanin babu kowane irin cigaba daga yanayinsa. Nunfashi Sayd din ya sauke ahankali yace "Zamu dauki nauyin nema masa lafiya tin daga Nigeria har zuwa qasashen da sukeda manyan likitoci idan hakan zai muku" Ya qarasa maganar yana kallan Dr ismail din wanda ya fashe da kuka yana rintse idanuwansa baki a juye ba damar magana. Matarsa saurin kallansa tayi kafin ta dawo da kallanta kan Sayd din wanda yake kallansu cikeda yanayi na buqatan amincewansu. Numfashi ta sauke tana jin farin cikin hakan sbd lura da Dr ismail din ya gane koma su din su waye sedai kukansa daya sakata jin jikinta na mutuwa. Godia tayi musu cikin tsananin farin ciki da godewa Allah. Duk yanda sayd yaso magana da dr din kwata kwata ba dama sbd babu abinda zasu iya samu daga garesa sbd bakinma ko kadan baya haduwa bare yayi magana dan haka suna buqatan nema masa lafiya kafin komai sbd shine zai bude musu komai a yanda yake. Masaukinsu suka koma ya kira AZIZ yayi masa bayanin komai na cewan Dr ismail din bazai iya tahowa ba kaman yanda ya umarta a taho dashi sbd sosai yake cikin ciwon dan haka lafiyarsa zasu nema dan samun biyan buqatansu. Kwana uku su sayd suka kwashe a jos kafin aka gama shiri a familyn dr ismail din suka taho lagos dashi tareda matarsa da qaninsa babba sbd jinyarsa. Suna isowa wata lafiyayyar asibiti aka kaisu take aka zubar da kudaden gaske sukace lafiyarsa suke so koda ta wuni daya ce indai zaiyi magana. Hakan kuwa akai take aka fara kulawa dashi a Amenity tareda tsaro babu abinda suka nema suka rasa, Matarsa da kaninsa ma duk abinda suke buqata an tanadar musu dan haka hankalinsi kwance suna fatar a dace da yiwa Sayd addua me tarin yawa sbd duk abinda ake basu taba sanin akwai wanda yake bayan taimakon nasu ba bare su sansa su iya sayd din suka sani sai Latif dayake kamar yaronsa. A bangare daya AZIZ zuciyarsa ta dena tinanin komai na duniya abu daya take buqata shine zancen da zai fito daga bakin Ismail akan Rasuwar Ummitah wadda baisan me zaijiba amma koma menene shi yake tsananin son ji fiyeda komai a duniya yanzu dan haka kudi sosai suke sakewa akansa. Ganin an dauki lokaci sai ahankali sai kawai ya umarci a fita zuwa italy gurin dr Nico da ismail din dan haka aka fara shirya tafiyarsu wadda cikin saa aka samu kallama komai a cikin wata daya suka tattara suka tafi harda matarsa da qanin nasa. Sati daya yayi a italy ya koma gida dan jiran labarin samun saukinsa daya tabbatarwa dr Nico koda na minti biyar ne yanason buduwan bakin ismail. *****A rayuwarsa wannan lokacin shine lokaci mafi nauyi a garesa sbd gaba daya baida abinda yake jira kaman dr ismail sbd jin yake kamar zaice masa Ummitah bata rasu ba tana duniya dan haka ganin an dauki lokaci babu wani cigaba sosai sedai yana samun sauki ba laifi sosai maganar ce kadai da motsa gabban jikinsa basa aiki. Zuciyarsa ta kasa dauka,kansa ya dauki zafi ya riqe nasa ciwon na neman dawowa na trauma dan haka kai tsaye ya kira Sayd yace ya siya musu ticket na tafiya italy. Rana tsaka dr Nico ya gansu cikin nutsuwa ya gama yiwa AZIZ din bayanin cigaban da ake samu na lafiyan dr ismail din. Shiru AZIZ yayi bayan ya gama sauraron dr ya nufi gurin ismail din ya zauna yana facing dinsa tareda zuba masa idanuwansa yana kallansa tsawon mintina. Numfashi mara sauti ya sauke kafin ya miqe ya fice. Kwanakin da zasuyi bai iya yinsu ba ya koma gida sbd Bazai iya tsayuwa a gaban mutumin da ransa yake rawaba ya tambayesa abinda bama zai iya fada da bakinsaba. A ranar da suka isa shima dr ismail din jin yayi kaman duniyar zai bari dan haka a sanyaye yake ko idanuwansa bayason budewa wanda hakan ya saka jikin matarsa sanyi tayita kuka tana rasa yaya zatai da ranta. Da daddare sayd ya iso palonsa ya tarardashi zaune yayi shiru fuskansa tayi fayau wanda ya saka Sayd jin jikinsa yana sake mutuwa sedai kuma kaman yanda Dr Nico ya kira yace ismail din zai iya amsa tambaya kowace iri batareda ya bude baki ba sbd idanuwansa suna motsawa ya sakasa yanke shawarar fuskantar komai a yau din dan haka ipad dinsa da fuskan dr Nico take bayyane ismail na gabansa zaune akan kujeransa dauke da belt ya ajiye a gaban AZIZ din wanda ya dago idanuwansa da sukai ja ya sauke akan screen din yana zubawa ismail din su yanajin zuciyarsa na wani irin nauyin gaske.... Sayd ne ya bude baki Ahankali cikin tsananin nauyin kirjin shima yace "A ranar da Ummitah ta haihu a asibitin zaadens da kanta haihu ko cs akai mata???? Rintse idanuwa ahankali dr ismail yayi hawaye masu zafi da baqin cikin rayuwarsa suna gangaro masa ya bude idon tareda kyaftasu ahankali alamar da kanta ta haihu........ Daukewa numfashin AZIZ ya kusa yi sedai bai motsaba Sayd da kafafunsa suka kafa rawa bude baki ya sake yi bugun zuciyarsa na tsananta yace "Meye aikin da kukai mata a kirjinta wanda batada shi???? Qarasa tambayar yayi muryansa na tsananin rawa..... Ahankali cikin tsananin sanyin jiki dr ismail ya gangaro da idanuwansa zuwa setin kirjinta AZIZ gurin zuciyarsa ya lumshe idanuwansa ahankali wasu hawayen na gangaro masa masu tsananin zafi....... Kasa magana sayd yayi sbd zuciyarsa data dena bugawa...... Dr Nico ne yayi saurin kallan ismail din da rawar murya cikeda tsananin tashin hankali yace "Zuciyarta aka cire????? Rintes ido yayi alamar hakan "Kun sakawa wani???? Sake rufe idanuwansa yayi amma kafin yama gama rufewa AZIZ ya miqe ya nufi kofa sedai ko taku daya yayi yana yin na biyu kafafunsa suka gasa sukai wata irin mummunan sarewa ya fadi a gurin. #MAMUH #BEST REVENGE #BROTHER's LOVE #AZIZ AY LIMBA #SELFMADE BILLIONAIRE #JANNAH ZAD ZAFAFA BIYAR KALBIM 500 mamuhgee A DUNIYATA 500 Huguma AJIYA A DUHU 500 Billyn Abdul KIRJIN ME HANKALI 500 Miss xoxo Pay at 0022419171 AccessBank Maryam sani gummi Shedan biya 09033181070 Or mtn vtu at 09032345899*_Arewabooks@Mamuhgee_* 42 *KALPANAH COLLECTION* 08105064494 Shin ke daliba ce ko kuma uwa wadda har yanzu bata daina rokon urgent 2k a wurin yan uwa da kawaye ba,tou nesa tazo kusa domin kuwa na kawo miki maganin matsalarki,domin kuwa *Kalphanah Collection* ta shirya tsaf domin taimaka wa duk wani dan kasuwa ko kuma wanda yake son fara kasuwanci.A *Kalphanah Collection* muna saida kaya kama daga Jaka,Takalmi,Atamfa,Laces,Kayan yara da kuma kayan kitchen.Wani abun mamakin ma muna saida kayan mu ga masu siyen daya ko kuma sari,ga waenda basuda jari ma mun tanadar masu hanyoyi daban daban da zasu fara neman na kansu.Hajiya kina gida kwace zaki dinga jin saukar kudi a asusun bankin ki.Ga musu fuskantar qalubale a kasuwancin su kuma an kawo muku sauqi domin kuwa an bude muku group dinku da zaku dinga tattauna matsalolin ku. https://chat.whatsapp.com/IyDlSVdw1rDIlCNNQMel68 Kedai idan kin shirya ki dannan link din nan na kasa domin shiga group dinmu ki ganewa idonki kunsan ance gani ya kore JI Karki yadda ki wuce bakiyi joining group din nan ba domin kuwa yanzu sallah tana qaratowa ko bakiyi kasuwanci ba zaki siya domin amfanin ki na yau da kullun kuma ko baku buqata yanzu nan gaba zaku iya neman ta. Siyen na gari maida kudi gida. 08105064494 ************* Sayd ma cak bugun zuciyarsa yake neman dakatawa sedai kuma halinda AZIZ yake cikine ya sanyashi yi kansa da tsananin sauri baya gani sosai sedai kafin ya isa garesa Tini hancinsa yafara gangaro da jini idanuwansa na rufewa sbd duk jarumtarsa da karfin zuciyarsa bai iya riqe abinda ya dakesaba harya saka jini balle masa ta hanci.... Da jahilin gudu sayd ya rarumo tissue gaba dayanta ya fasa box din ya zazzageta ya damqa yana tare hancin AZIZ din wanda baya jin komai kunnuwansa da idanuwansa sun dauke wuta. Da gaggawa Ya fito dashi bai tsaya komaiba ya saka mota yabar gidan dashi cikin tsananin gudun gaske. Fiddausi dataga fitowansa da AZIZ din jikinsa jini sosai sbd bleeding yake sosai take ta saki tray din hannunta dayake dauke da tea set da dabino dayake cikin bowl me kyau tana qarasawa cikin office da mugun gudu taga jini a tissue koina.... Ihu ta kurma wanda ya saka mama fitowa da sauri Falaq data mugun firgita ma bayan maman ta biyo tana roqe rigar maman sbd tsoro suka nufo office din. Da gudu Fiddausi ta kwaso tissues din da hannunta a rikice ta nufo su maman tana nuna mata jinin dayake jiki sosai bakinta na rawa tace "Sir LIMBA ne Sayd ya fita dashi jini yana fita jikinsa sosai baya numfashi kaman ba rai a jikins...... Bata qarasa ba Falaq dake bayan mama cikin tsoro ta fito tana kallan hannun Fiddausin muryanta na rawa sa sauri tace "Daddyna?? Meya samesa? Meya faru dashi?? Kikace ya mutu....?????? Bata qarasa ba ta kirjinta yayi mummunan bugawan data yanke musu jiki a gurin tai collapsing. Sabon tashin hankali suka shiga wanda ya saka mama duk rudewa tana cewa "Uban waye yace ki kafa a gabanta ne Fiddausi" Daukanta Fiddausi tayi da duka karfinta tana nufar cikin gida da ita mama na bin bayansu tana kwalawa Nena kiran ta kawo musu ruwa da sauri. A palo suka kwantar da ita nena ta kawo ruwa da sauri suka zuba mata amma sam ba alamar zata tashi hankali tashe suka dauketa zuwa asibiti mama nata kiran Sayd sedai sam baya dagawa sbd baima san tana kiranba sbd koda ya isa asibiti AZIZ ya zubarda jini sosai dan haka take aka karbesa da gaggawa akai ciki dashi sbd shock ne da attack daci uban wanda ya shiga ko lokacin da ya samu labarin rasuwarta. Sosai hankalinsu dr Raheem ya tashi sbd kokarin ceto Ransa da suke sedai baya alamar yana karban treatment din dan haka suka sauya method cikin gaggawa kwarewa. Sayd kuwa ana shigewa da AZIZ din zubewa yayi gurin a qasa yana cusa kansa cikin kafafunsa tareda fashewa da wani irin kuka me karfin gaske yana dukan kirjinsa dake wani irin azababben radadi da ciwon kwatanta azabar da Ummitah ta shiga kafin rasuwarta, Da ranta aka zare mata zuciyar datake bugawa a kirjinta batareda wata nakasa ba, Da karfi da yaji aka zare mata zuciyar da Allah ya halicceta da ita, Kasheta akai kisa mai ciwa da radadi batareda taga ko abinda ta haifa da kanta ba.... Wani gawurtaccen kukan ya sake sakewa radadin da zuciyarsa da kirjinsa ke masa suna tsanantar da shima ya kasa riqewa ya fara dafawa zai miqe sedai gangar jikinsa kasawa tai ya zube a gurin yana fasa kukan dayake fitowa tin daga tsakiyar zuciyarsa dayakejin inama tasa zuciyar aka cire aka bar Ummitah da tata. Gaggawan zuwa akai shima aka kwashesa zuwa emergency sbd ganin irin yanda namiji babba kuma kakkarfa kamarsa da bai rasa komai na jin dadin duniyaba yana kuka sosai yana shidewa ga gangar jikinsa tana kasa daukansa. Ana shigewa dashi su mama na isowa asibitin da falaq wanda itama aka karbeta sbd patient dinsu ce dan haka baa shiga emergency da ita ba ita dakinda zaa kwantar da ita aka nufa da ita da sauri acan suka fara bata taimakon gaggawa duk da sunsan abune me wuya ta farfado yanzu din. Su mama da basusan nan asibitin su AZIZ suke ba zaman jira suka fara cikin tashin hankali da damuwa kala kala kuma har lokacin bata dena kiran wayar Sayd ba. Rin suna zaune har suka kasa zaman sai kaida kawo suke, shima suka gaji suka fita suka dawo babu zancen komai hakama ba bayanin komai akan AZIZ. A asibitin suka kwana cikin masifaffen tashin hankalin daya gama rikice musu.. Guraren 6 na safe Sayd ya farfado cikin hayyacinsa ya tashi zaune yana rintse idanuwansa sa sukai tsananin nauyi da kansa. Ya jima a zaune nurses na sake dubasa kafin dr Raheem yazo ya sake dubasa ya sanar dashi Falaq na asibitin tin daren jiyan itama aka kawota. Yanajin hakan ya dago da sauri sbd take yasan ansake triggering ciwonta kenan.. Saukowa gadon yayi ya nufi toilet din dakin cikin karfin hali da jarumta yayo alwala ya fito a dakin yayi sallah. Yana gama addua ya dauki wayarsa dake gefen gadon yaga kiran mama sunfi guda hamsin. Miqewa yayi yana sallamar kansa ya fice daga dakin ya nufi gurinsu mama wainda suna ganinsa Fiddausi ta miqe tsaye tana zuba masa duka idanuwanta jiran abinda zai fada. Mama kuwa da tini itama ciwon zuciyarta yaketa kokarin tashi sbd tashin hankali da damuwa kasa tashi tayi daga zaunen ta zuba masa idanuwanta da sukai ciki sbd damuwa da rashin baccin da sukai a daren. Muryansa datai tsananin nauyi sbd yanayinsa ya bude baki yace "Mama yaya falaq? Meya sameta?badai collapsing tai ba?? Mama data rasa wace tambayar zata amsa tace "Daddynta dataji ba lafiya ta zube,ina AZIZ din?yaya yake,meya samesa?? Shima a qataice ya amsa tambayarta da cewa kawai attack ne ya samu amma insha Allah zuwa yanzu ma ya samu dawowa daidai. Juyawa yayi ya nufi dakin da falaq take yaga tana kwance sanyeda wasu abubuwa da aka daura mata. Rintse idanuwansa yayi yanajin wani irin nauyi da qunci na danne kirjinsa na tinawa da suna tsaye a kofar dakin da ake ciki ana cirewa Ummitah zuciyarta suna gadin banza batareda sun saniba a wancan lokacin... Juyawa yayi da sauri yabar dakin ya nufi waje gaba daya ya isa mota ya bude ya fada tareda rufewa yana dora kansa a steering yana dafe kirjinsa da hannuwansa duka biyu sbd ciwon dayake masa sosai.. A wannan lokacin da ake cirewa Ummitah zuciyarta da abu ne da Allah zai nuna musu zai fasa kofar dakin ya shiga ya cinnawa gabaki daya likitacin dake ciki wuta batareda ya bar hakan ba dan zai iya tada asibitin gaba daya daya bari a taba ko kirjin Ummitansa bare rabata da ranta karfi da yaji. Dukan kirjinsa yake da karfi idanuwansa na cika da hawayen da suka qafe sunma kasa gangarowa sbd radadin dayake cikinsa. ****Acan ciki kuwa Karfe goma AZIZ ya bude idanuwansa ahankali da suke jajir kamar wanda yayi shekara a cikin matsanancin hali... Akan fuskan Mama datake zaune a dakin ya sauke idanuwansa batareda ya kyafta ba, Tasowa mama tayi ahankali tana kallansa cikeda fargaban ganin jan idanuwansa. Bakinta ta bude cikeda tsananin kulawa da kauna zatai magana ya rigata a hankali da wani irin sauti me tsananin sanyi da rashin hayaniya yace "Mama wani irin kewana Ummitah tayi a lokacin da bana nan kafin kafin rasuwarta, Wane irin yanayi ta shiga a lokacinda ciwon ajali ya taso mata??? Cak mama ta tsaya cikeda matsanancin mamaki da tsoro sbd tinda akai rasuwar a tsawon shekarun bai taba ambatar kalma daya data danganci rasuwarta ba bare yanda ta rasun suma sunyi shiru sbd bai taba tambaya ba ko maganar sai yanzu kwatsam taji tambayar kamar saukan aradu.. Dago idanuwanta tayi ta kallesa shima ita yake kalla har lokacin batareda komai ya motsaba a jikinsa wanda ya saka gaban mama mugun faduwa tana nufosa da sauri sbd tsoron idan ba paralys dinne ya kuma samu ba. Hannunsa ya daga ahankali ya dakatar da ita yana rintse idanuwansa sbd bayason motsawa ko kadan sbd wutar datake cin jini da gangar jikinsa tareda zuciyarsa. Dakatawa tayi tareda zaunawa ahankali kan kujera idanuwanta na dan sauyawa sbd itama harga Allah batason tina rashin Ummitan da sukai. "Kafin tasowan nakudarta tinda kabar qasar Ummitah bata taba samun lafiya ko sauki ko kadanba, Ciwone yake cinta wanda muka rasa gane kona mene, Rama takeyi jininta na tsotsewa tana komawa ba kyan gani, Bata iya ci bata iya sha,bata iya yiwa kanta komai sai yanda akai da ita, Duka wannan ciwon a jikinta yake amma a zuciyarta kaine kadai abinda zuciyarta ke tsananin buqatan gani da kasancewa sedai mun hanata barin kasan halinda take ciki sbd kada hankalinka ya tashi amm......... Wasu hawayen da babu wanda ya taba ganinsa dasu ne duk duniya suka gangaro masa ya rintse idanuwansa yana damqar bargon dayake rufe da jikinsa wata irin wuta me tsananin zafin gaske tana cin zuciya da gangar jikinsa.... Cigaba mama tai itama idanuwanta na gangarowa da hawaye sbd yaune ranar data samu damar fadar ciwonta da radadinta na rashin Ummitah tareda shi hawayenta na saukowa bayan shekaru itama tace "Ummitah ta rasu da tsananin ciwon rashin ganinka ko jinka, Ta tafi batareda ta saka abinda ta haifa tabari ba, Ta tafi da tsananin tausayinka bana kanta ba, Kaine damuwarta,kaine a ranta,kaine a tinaninta kaman tasan tafiya zatai tabarka.... Kasa cigaba da magana maman tayi ganin yanda yake kuka sosai abinda bata taba gani ba a rayuwarta, Tin yana yaronsa Allah yabasa wani irin karfin halin da baya kuka hakama duk gwagwarmayar daya shiga ta rayuwa baya kuka amma ayau kuka yakeyi sosai dukkanin jikinsa na jijjiga. Kukan takeyi itama sosai na tsananin tausayinsa sbd tana kwatanta irin radadi da azababben ciwon dayake ji.. Sayd da Fiddausi da fahad daya iso tareda dr Raheem da suke kofar dakin dukkaninsu tsayawa sukai jigum jigum babu me motsawa zuciyoyinsu na sanyi da shiga wani irin damuwa da tsananin tausayinsa sbd suna jin kukansa daya saka gabaki dayansu tsikar jikinsu tashi sbd yau ne Allah ya basa ikon fasa kukan rashin Ummitansa wadda sun san tsawon shekarun nan ciwo da gyambon hakan na nan a tsakiyar zuciyarsa sai yau Allah ya basa ikon fashewa tinda ya samu ya fasa kuka. Fiddausi ma kasa riqe kanta tayi kukan takeyi sosai mara sauti sbd tsananin tausayi da yanda su kansu rashin ya dawo musu sabo. Fahad ma hawayen ne suka cika idanuwansa sedai basu saukoba, Sayd jajir idanuwansa sukai ya sunkuyar da kai kukan AZIZ din na ratsa zuciyarsa yana yankawa.. Dr Raheem kuwa sanyi jikinsa yayi sbd jin kukan wanda yake ganin yafi duk wanda ya sani taurin zuciya da kamewa a rayuwarsa dan haka shima ya kasa shiga sbd wannan moment din babu wanda ya kamata ya kasancesa idan ba mahaifiyar tasa ba wadda ita kadaice a ciki kuma ita kadaice ya kamata taga kukansa. #MAMUH #BEST REVENGE #VILLAINS ARE MADE NOT BORN #AZIZ AY LIMBA #ZAADENS ZAFAFA BIYAR KALBIM 500 mamuhgee A DUNIYATA 500 Huguma AJIYA A DUHU 500 Billyn Abdul KIRJIN ME HANKALI 500 Miss xoxo Pay at 0022419171 AccessBank Maryam sani gummi Shedan biya 09033181070 Or mtn vtu at 09032345899*_Arewabooks@Mamuhgee_* 43 *ZUZEAM VENTURES* Best APHRODISIAC (kayan mata) 08144015291 Aslm barkanmu da wannan lokaci Ina Mai farin cikin sanar daku cewa Zuzeam ventures takawo maku ingantattun magunguna masu inganci cikin Aminci Muna da kaya kamar haka Mallaka Maganin sanyi Maganin cire tumbiMaganin farin jini Maganin matsiMaganin mata Maganin sa ni’ima da dandano Dulka Amare Set na gyran jiki Set na amarya Tabaje tsumin Gomba Xuma kiba ta hips and Brest Magungunan gyran Brest Magungunan Karin hips Maganin sliming Muna da kaya masu inganci cikin sauki da rahusa Ina wadda keneman mallaka sahihiya quaranty wlh hajiya kixo ga zuzeam ventures xakiji ddin mallaka duk fadin ran ogah duk fadansa wlh sai yyi sanyi 08144015291 Idan maganin mata kikeso akwai Idan gyran jiki kikeso gyran fata gyran Brest magungunan sa kiba da hips DOMIN samunta Kai tsaye kira wannan no 08144015291 DOMIN mgn da ita whatapp 08144015291muna tura kayanmu ko ina cikin iKon allah 🥰👌🏻 Bononza Bononza Tsimin mangoro 1k🥭 Tsimin dabino 1k Gumba ukku balai 700 Gumba aya da nonon rakumi 700 Garin kafi ciccibi 500 Garin bata gaban kishiya 500 Matsin mallaka tada zaune tsaye 2500 Turaren mallaka ba aba mai kishiya 2500 Total kayan 9500 Za a bakisu akan 4200 Kuma mutun goman farko nadakyautar Abun 2k 🗣️🗣️🗣️🗣️🗣️🗣️ ASSALAMU ALAIKUM ALHAMDULILLAH YAN UWA NEW PROMO YA KAMMALA💃🏽💃🏽💃🏽😁😁😁 da 6k dinki ki kwashi kayan 12k hajiyata 💃🏽💃🏽💃🏽😃🙃Kazar gadali ta mallara Rabi 3500 Tsimin gam gam 1500 Ruwan kara zunzurutun dadı😋800 Garin 7in1 1k Gumba 3 balai 500 Gumba kwakwa da dabino 500 Na Infection 1k Garin zunzurutun dadi 1200 Matsin ba a fira d wando 500 Matsin infection mai matse mace gam 500 12k All at 6k https://wa.link/l1gcz8 kedai dannan link dinnan don samun naki ki maza kiyi bucking koda kudinki saida Rabonki **************** Sun dauki lokaci sosai ahakan babu wanda ya iya doguwar motsi zuciyoyinsu a jagule da damuwa da mutuwar jiki, Dr Raheem ne yabar gurin yabarsu suji da damuwan dayake damunsu gavaki dayansu sbd ya lura matsalar ta taba zuciyoyin kowa a familyn dan duka kallan family daya yake musu wanda kaf dinsu basu hada alaqar jini ba kawai kaunace data hadu ta zama kamar jini daya da babu sirki. Sayd yafisu zama abin tausayi sedai yafisu karfin halin riqewa a zuciyarsa kansa na sunkuye har aka dauki lokaci sosai kafin sukaji tsit a dakin babu sauti komai bayan mama tagama fayyace masa labarin yanda sukaita fama da yanda dr ken ya turasu zaadens hospital ta qarasa fayyace masa cikin radadin tinaw da ranar har saida takao ta kasa cigaba da magana ta bude kofar dakin ta fito idanuwanta jajir tana share fuskanta da tissue ta janyo kofar dakin ta rufe tana bude baki a sanyaye tace abarsa shi kadai tukuna. Wucewa tayi zuwa dakin Falaq ta zauna tana sauke ajiyan zuciya wani abu daya danne kirjinta da dadewa taji ya yafa mata sbd daga karshe yau dai tayi maganar Ummitah da AZIZ wanda takejin sassaucin ya zai samu sassaucin shima tinda ya samu ya furta kuma ya saurara. Fiddausi ma datasha kuka sosai a sanyaye ta shigo dakin ta nufi toilet ta wanko fuskanta ta fito ta zauna tana duba wayarta da akaita kira batama saniba. Acan ma fahad barin asibitin yayi ya koma office Sayd kawai aka bari kofar dakin zaune shiru. Wutace ta gama cinye zuciyarsa tas yakeji ta tsananin qi da zafin Zaadens da baida tabbacin a cikinsu wayene zuciyar Ummitah take bugawa a kirjinsa duk da suna zargin JANNAH ZAD ce sedai kuma ba lallai ita din bace da kuma son sanin waye Dr zad din da ake fada amma dai koma waye aka kashe Ummitah dan a rayasa tabbas bazai taba farin cikiba a rayuwarsa. Wuni guda babu me shiga dakin da AZIZ din yake har Sayd kuwa sbd ya hana kowa ya shigowa garesa bayan dr Raheem wanda ya sallamesa dan haka babu wanda ya gansa saida ya bude kofar dakin ya fito da kansa sanye da kayan sanyi tareda fcap da facemask daya rufe fuskansa. Ahankali yake takawa cikin nutsuwa Sayd ya taso yana masa sannu tareda fahad wanda shima ya sake dawowa. Mama ma da Fiddausi sannun sukai masa babu wanda ya amsawa da baki sai kansa daya dagawa kowa a hankali cikin nutsuwa suka nufi mota batarea da ansanar dashi falaq na asibitin ba sbd kada abin yayi masa yawa. Sayd ne ya bude masa mota ya shiga ya rufe tareda zagayawa ya shiga gaba fahad kuma ya shiga mazaunin driver ya tada motar suka fice daga asibitin motar tsit ma sauti komai saina ac dayake ratsa kowannensu. Suna isa gida da daddare ne dan haka parking kawai fahad yayi ya fito ya bude masa motar ya fito ahankali ya wuce ciki batareda ya iya cewa komaiba.. Daidai yana gap da shiga palo wayarsa dake hannun sayd tayi ringing, Sunan Dr Nico sayd din ya ambata wanda ya saka AZIZ din tsayawa cak batareda ya juyoba yana dan rufe idanuwansa da babu abinda yake cikinsu sai azabar zafin da tiririn wutar dake ci a zuciyarsa da jininsa. Qarasowa Sayd yayi tareda daukan wayar ya saka handsfree batareda AZIZ din ya karba ba. Cikin sanyi dr Nico yace "Jikin Ismail ya rikice gabaki daya bayajin lallai ismail din zai tashi sai wani ikon Allah, Amma kafin ya rikice din a jiya bayan kun kashe waya ya bada wasu bayanai ta hanyar motsawa da hannuwansa...." Dan Shiru yayi sbd tinanin yanda AZIZ zai karbi zancen tinda shine likitansa yasan halinda suka shiga gurin treating nasa wancan karan daya samu paralys daqyar sukaga Allah ya nuna ikonsa akan AZIZ din ya tashi dan haka yake kiyaye abinda zai fada masa akan Kanwar tasa. Ahankali ba zato sukaji muryan AZIZ din ya furta "Babu abinda zuciyana bazata iya daukaba a duniya yanzu,just go ahead and say it" Numfashi Nico ya sauke yana cigaba da cewa "Ya bada tabbacin Cire zuciyarta akai bayan ta haihu da kanta kuma lafiya kalau sedai already koda aka kawota asibitin kusan brain dinta yagama mutuwa sbd ba aranar aka fara shirin cire zuciyartaba ahankali sun kashe brain nata, Zuciyar na zaadens tana bugawa a kirjin wani daga cikinsu wanda bai samu nuna waye ba a cikin hotinan zaadens din dana nuna masa jikinsa ya rikice sbd brain dinsa da zuciyarsa bazata iya daukan pressure din zancen ba dan haka idan akwai abinda kuke buqata dashi kuzo kafin time dinsa ya cika" Wani boyayyan numfashi AZIZ din ya sauke mara sauti numfashinsa na cunkushewa yayi gaba batareda yace komaiba. Sayd ma wayar ya kashe yana bin bayan AZIZ din wanda yana shiga palonsa ya rufo kofar yana jingina bayansa jikinta ya rintse idanuwansa dake radadi yana dora hannunsa setin zuciyarsa dake tsananin ciwo da radadi ya gurfane gurin yana cusa kansa cikin qafafunsa kamar qaramin yaro yana jin tsananin sanyin rayuwarsu ta baya da suke rayuwa a cikin mataccen gidansu yana dawo masa tareda mahaifiyarsa da Ummitah tana qarama. Rawar sanyi jikinsa keyi yana kakkarwa sosai yana tinano dumi na jikin Ummitan idan tana jikinsa a lokacin sbd bata kariya daga sanyi rungumeta yakeyi sanyin yana shigewa shi a jikinsa...... Wasu zafafan hawaye masu radadi ne suka fara biyo gefen Idanuwansa yana jin kewanta na kashe kowane lungu da sakon tasa zuciyar. Sayd dayake bakin kofar jin yayi karar fasa kayayyakin palon taka tashi da karfin gaske tareda kukansa dayake yaga tasa zuciyar. Gwiwowinsa Sayd yakai kasa a kofar palon yana sunkuyar da kansa idanuwansa na sake sauyawa zuwa jajir yana jin kaman ya bude ya rungume AZIZ din ko zai samu kashe masa wutar datake ci a zuciyarsa amma ba damar hakan sbd yasan a wannan lokacin ko kusantarsa wani yayi zai iya rabasa da ransa fit dan haka yakejin radadin AZIZ din har tasa zuciyar. Duk abinda yake palon babu abinda ya bari da sauran amfani sbd ya fasa komai hannuwansa jini sukeyi sosai sbd glasses da suka yankesa koina amma sam bai damu ba a hakan ya zube qasa ya kwanta yana rufe idanuwansa yana jin buqatar bugawan zuciyarta a hannunsa,baa kirjin koma waye takeba a hannunsa yakeson karbota ya rabata da kirjinda aka kashe Ummitansa akai, Bazai taba jin abinda yake tokare da kirjinsa ba ya fada sai ranar da zuciyar Ummitah ta sauka a hannunsa yakai kabarinta ya rufe mata ita dik da babu abinda ya rage a gangar jikinta amma zai kai mata zuciyar kabarinta ya rufe mata ita. Koma waye aka raya bayan kashe tasa yar uwar zai tabbatarda da hannunsa zai ciro ya basa abarsa a hannunsa, Duk wanda ya taba hada ko hulda d zaadens saiya tabbatarda duniya ta dena masa dadi kwata kwata, Daya bayan daya saiya rabasu da abinda sukafi so a duniya duniya ta hanya mafi munin da zata sakasu kashe kansu da kansu. Yana kwance a gurin cikin jini idanuwansa a rufe bai iya ko motsawaba har asuba.... Kiran asuba ya sanyasa bude idanuwansa da sukai jajir ya miqe tareda nufar bedroom dinsa kai tsaye ya nufi toilet ya sakarwa kansa ruwan zafin da hayaqinsu ahankali ya ciked toilet din ya lumshe idanuwansa ruwan na ratsasa yana jin kansa sabon mutum. Hannuwansa da jini ya bushewa ya zubawa idanuwansa jinin na wankewa da kansa yana zubewa qasa tareda duk wani sauran tausayinsa da tsaftar zuciyarsa dan ko qanqanin tausayi da jin qai jin yayi yana ficewa daga jininsa da zuciyarsa. Fitowa yayi daga toilet daure da brown towel lafiyayyar kakkarfan jikinsa na daukan ido a hasken lafiyayyan dakin da babu abinda ya rasa na luxuries da jin dadin rayuwa. Fararen hoodie Sweatset na Ralph Lauren ya saka ya fito da hular zanyi me kauri sosai akansa ya fito dan zuwa masallaci. Yana bude palonsa Sayd dayake zaune bakin kofar yayi saurin miqewa yana kallansa. Yanayinda Sayd ya gansa ne qamshi me dadi yana fita jikinsa ya sakasa shiga mamaki sedai kuma kwayar idonsa daya yiwa kallo daya take yasan sabon AZIZ AY LIMBA ne a gabansa dan haka ba bata lokaci ya buda baki zaiyi magana LIMBAn ya katsesa da muryansa me cikeda kwanciyar hankali da izza yace "Ka shiryo muje sallah" Juyawa Sayd yayi yaje dakinsa yayo alwala ya sauya kayansa shima zuwa kaya masu dan kauri da hula suka fice. AZIZ dinne yaja motar har zuwa masallacin. Ana gama sallah ya jima yana addua sosai kafin suka fito. Suna isowa gida Geam kai tsaye ya nufa yana zare rigar jikinsa me kauri ya jefar a yana shiga makeken geam dinsa dayake cikin gidan dagashi sai black vest din datake jikinsa yafara geamin yana sauraron sayd dayake tambayarsa yanda zaayi da dr ismail. Baici komaiba saida ya dauki lokaci yana abinda yake kafin ya dakata yana daukan towel yafara goge zufan dayaje gangara akan lafiyayyar fatarsa ya kalli Sayd din yace "Kafara kiran center din da ake neman heart donors ka shigar da akwai wanda zaiyi donor ga wanda yake kan layin neman donor na zuciya da qoda, Kana gam wannan ina buqatan bin jirgin zuwa italy din dan saka hannun wanda zaiyi donor din da kansa ba tirsawawa, Idan ka gama wannan a fara shirye shiyen komawanmu gida Nigeria gaba daya lokaci yayi" Yana gama fadar hakan ya saka kai ya fice yana mamakin jin shirun gidan ba hayaniyar Falaq Aziz dinsa. Yana ficewa mutuwar tsaye Sayd yayi cikin mamaki sedai kuma hakan shine abinda yake jira dan haka cikin samun satisfaction da sabon AZIZ LIMBA ya ciro wayarsa aljihunsa dan kuwa ayau zai gabatarwa da masu neman sadaukarwan zuciya da koda an samu me saudaukan da kansa a kyauta dan yasan a ruwan sanyi dr ismail zaiyi sadaukarwa me amfani ba tirsasawa a natse wanda nasa sassaucin kenan ya tafiyarsa ya huta bayan ya girbi abinda ya shuka tukuna manyan shegun. #MAMUH #BEST REVENGE STORY #BESTLOVE #HOTLOVE #HATE/LOVE STORY #SACRIFICE ZAFAFA BIYAR KALBIM 500 mamuhgee A DUNIYATA 500 Huguma AJIYA A DUHU 500 Billyn Abdul KIRJIN ME HANKALI 500 Miss xoxo Pay at 0022419171 AccessBank Maryam sani gummi Shedan biya 09033181070 Or mtn vtu at 09032345899*_Arewabooks@Mamuhgee_* 44 *ZUZEAM VENTURES* Best APHRODISIAC (kayan mata) 08144015291 Aslm barkanmu da wannan lokaci Ina Mai farin cikin sanar daku cewa Zuzeam ventures takawo maku ingantattun magunguna masu inganci cikin Aminci Muna da kaya kamar haka Mallaka Maganin sanyi Maganin cire tumbiMaganin farin jini Maganin matsiMaganin mata Maganin sa ni’ima da dandano Dulka Amare Set na gyran jiki Set na amarya Tabaje tsumin Gomba Xuma kiba ta hips and Brest Magungunan gyran Brest Magungunan Karin hips Maganin sliming Muna da kaya masu inganci cikin sauki da rahusa Ina wadda keneman mallaka sahihiya quaranty wlh hajiya kixo ga zuzeam ventures xakiji ddin mallaka duk fadin ran ogah duk fadansa wlh sai yyi sanyi 08144015291 Idan maganin mata kikeso akwai Idan gyran jiki kikeso gyran fata gyran Brest magungunan sa kiba da hips DOMIN samunta Kai tsaye kira wannan no 08144015291 DOMIN mgn da ita whatapp 08144015291muna tura kayanmu ko ina cikin iKon allah 🥰👌🏻 Bononza Bononza Tsimin mangoro 1k🥭 Tsimin dabino 1k Gumba ukku balai 700 Gumba aya da nonon rakumi 700 Garin kafi ciccibi 500 Garin bata gaban kishiya 500 Matsin mallaka tada zaune tsaye 2500 Turaren mallaka ba aba mai kishiya 2500 Total kayan 9500 Za a bakisu akan 4200 Kuma mutun goman farko nadakyautar Abun 2k 🗣️🗣️🗣️🗣️🗣️🗣️ ASSALAMU ALAIKUM ALHAMDULILLAH YAN UWA NEW PROMO YA KAMMALA💃🏽💃🏽💃🏽😁😁😁 da 6k dinki ki kwashi kayan 12k hajiyata 💃🏽💃🏽💃🏽😃🙃Kazar gadali ta mallara Rabi 3500 Tsimin gam gam 1500 Ruwan kara zunzurutun dadı😋800 Garin 7in1 1k Gumba 3 balai 500 Gumba kwakwa da dabino 500 Na Infection 1k Garin zunzurutun dadi 1200 Matsin ba a fira d wando 500 Matsin infection mai matse mace gam 500 12k All at 6k https://wa.link/l1gcz8 kedai dannan link dinnan don samun naki ki maza kiyi bucking koda kudinki saida Rabonki ********* Bedroom din Falaq ya nufa kafin ya qarasa su mama da suka dawo suka shigo palon suna sauke ajiyan zuciya da samun nutsuwar Falaq din data farka tin asuba kuma ta daga musu hankali dan haka tinda ba wani ciwo suka dawo gida tareda ita bayan dr Raheem yace ba damuwar komai. Da gudu tayo gurinsa tana fashewa da kuka ta fada jikinsa tana cewa "Daddy dan Allah karka sake rashin lafiya banason komai ya sameka" Rungumeta yayi yana kallansu mama sayd daya shigo ya kalleta yana cewa "Yaya jikin nata mama? Cikin sauke numfashi da ajiyar zuciya mama tace "Gatanan ta miqe ta ishemu da ragamar zuwa gurin Daddynta" Da mamaki yake kallansu kafin ya dagota daga jikinsa yana kallan fuskanta zuwa jikinta tukuna ya dago ya kallesu yace "Did she collapse again?? Gyada masa kai Sayd yayi da cewa "Amma komai insha Allah yana under control dr Raheem ya kira yace is not that serious so ba lallai ta kai wancan matsayinba" Dawo da kallans yayi kan falaq din wadda take lafewa jikinsa ya dago fuskanta cikeda kulawa da tsananin kauna yace "Ki dena daga hankalinki a komai na rayuwa, Babu abinda zai samu Daddynki insha Allah amma idan wani abu ya sameki I can't take it..... Rungumesa tayi har lokacin tsoron abinda ya samesa bai gama sakinta ba dan sosai ta shiga firgitan da bata taba sanin yaya yake ba arayuwarta. Qanqamesa tayi muryanta na bayyanarda tsoronta tace "BestDaddy kar komai ya sameka dan Allah kaji?? Idan har wani abu zai sameka sbd nai maka alkawarin bazan sake barin komai ya sameniba insha Allah, Naji tsoro sosai da akace wani abu ya sameka Daddy.... Hawaye ne suka gangaro mata tana kasa riqe kukanta dayake cin ranta na tsananin firgitan datai dan ko kalman da Fiddausin ta fada ta tina jin take kuka na zuwar mata. Kukan data fasa dinne ya sakasa sauke numfashi yana miqawa Sayd hannu ya basa handkerchief yafara goge mata hawaye yana rarrashinta kafin ya jata sukai palonsa yana cewa 'Ya isa kukan Bestyn Daddy" Tsoki mama ta sake tana cewa "Lallai 'yar nan ta gama renamu, Muyi kwanan zaune a asibiti cikin sanyi da damuwa duk batace komaiba sai yanzu ta saka kukan ubanta" Fiddausi dai dataga tai fitar kutso na ganin falaq ta tashi wani abin bai sametaba akan labarin dataji a bakinta ajiyar zuciya ta sauke tana godewa Allah da komai ya dawo daidai a gidan sbd Shi kansa Uban gayyar Tamkar sabon mutum ne suka gani a gabansu sbd yanayinsa daya dan sauyu. Dakinta ta nufa tana kashe wayarta sbd ta dan huta kanta tsananin ciwo yake mata. Mama ma dakinta ta nufa bayan ta kwalawa Nena kira tace akai mata tea me zafi da madara sbd cikinta takeson gasawa sanyi takeji kaman ya shige mata koina har a ciki. Sayd kuwa ficewa yayi dan ayyukan dake gabansa sunada yawa ciki kuwa harda bawa zaadens damar ganin LIMBA kaman yanda suke buqata dan haka lokacin haduwarsu yayi na ganin juna da ganin irin matsayi da girman ikon da kowa yake dashi. A palonsa zaunawa yayi da falaq din ya rarrasheta tareda tabbatarda tsoron dayake ranta ya fice ya kama hannunta da kansa ya rakata har bedroom dinta ya shiga toilet dinta da kansa ya hada mata ruwan wanka yace ta shiga tayi. Da hannunta tai masa alamar ya sunkuyo qasa sosai. Kyakkyawan murmushin daya sakata godewa Allah da kamanninsa ta dauko ya sunkuyo batareda murmushinsa ya daukeba dan yasan me zatai. Gefen fuskansa tai kissing tace "I love you BestDaddy, Allah ya baka duk abinda kakeso duniya da lahira, Allah ya cika maka duk wani burin da kake dashi a zuciyanka" Fararen idanuwansa ya saukan a fuskanta yana kallan Ummitansa akan tata fuskan zuciyarsa na sosuwa sbd Adduar Ummitah kenan akansa tin tana yarinya itama. "Amin" ya furta ahankali yana shafa kanta kafin ya juya yabar dakin ita kuma ta tube ta fada toilet. Yana fitowa daga dakin kai tsaye Bedroom dinsa ya nufa zai shiga wanka sbd geam da yayi. Wayarsa datai haske ne alamar shigowan sako ya sakasa kallan wayar sakonne kuwa na dr Raheem na sabon report din Falaq din da aka turo masa. Bai taba wayarba dauke idanuwansa yayi akan sakon yana maidawa kan hoton UMMITAH dayake kan screen din wayar tana kauye lokacinda yayi mata shi kafin tafiyarsa daya dawo ya tadda an mata aure.... A kauye yayi mata shi sedai kaunar dayakewa komai nata sam bai damu da a kauye ko birni kokuma a waye ko a kauyence ba indai Ummitah ce a kowanne yanayi son dayake mata dayane ba banbancin ko sauyi. Dariya take a hoton tana kallansa cikeda kauna koda yayi mata shi.. Dauke idanuwansa ahankali yana nufar toilet ya shige ya zare kayansa tareda sakarwa kansa ruwan dumi yana rufe idanuwansa tareda dafa bango da hannunsa daya. Bai jimaba ya fito da towel a jikinsa ya tsaya gaban mirror yafara shiri dan shi baya zama gaban mirror kaman mace a tsaye yake shiryawansa. Karfe goma ya fito lokacin angama shirya table kusan kowa yafito dan haka yana fitowa kai tsaye dining din ya nufa kowa yana can already. Falaq na ganinsa ta taso daga gurin Sayd dayake nuna mata abu a waya suna dariya tana lafe gefen jikinsa Kaunar mahaifi da 'ya yana ratsa Sayd yana jin kaman ya bude cikinsa ya maidata sedai kuma kaman yanda ya fada ba shine mahaifinta ba AZIZ ne dan yabar masa ita duniya da lahira. Zaunawa sukai yana gaida mama da basu gaisaba a dazun sbd yanayin da aka samu kai. Amsawa maman tai tana tambayarsa jikinsa cikeda kulawa, Fiddausi data kawo tray din madarar data dafowa falaq cikeda girmmawa kanta a qasa ta gaidasa tareda barka da fitowa tana ajiye kayan hannunta gaban falaq. Breakfast suka fara cikin kwanciyar hankali da nutsuwa kaman yanda suka saba ba hayaniya ba surutu sai Sayd dayake amsa waya akai akai sbd tafiyar da zasuyi yau yana buqatan handling wasu abubuwan anan da kuma can dan haka ma ya riga kowa barin dining din yana waya da Agent kusan na Hudu da aka turo masa akan gidan da zasu siya a Nigeria. Suna gama breakfast din suka baro dining a palo suka zauna yana waya a natse kwarjininsa na cike gurin falaq na gefensa tana shagwaba sbd jin tafiya zasuyi da Uncle a yau din. Yana gama wayar mama ya kalla datake zaune tana duba abu a wayarta da glass dinta na qara gani duk tayi ciki da idanuwan tana dubawa a natse yace "Zamuyi tafiya, Idan na dawo zamu fara shirye shiyen komawa Nigeria insha Allah" Kallansa mama tayi tana ajiye wayar hannunta cikin mamaki da jin dadi sbd ta dade tana musu shaawan komawa sedai kuma sbd shi din bai taba hada niyar komawaba ya saka bata taba magana ba dan haka jinsa kai tsaye ya fada hakan sai taji farin cikin hakan dan kuwa jikinta na bata a Nigeria ne zasu samu yayi aure da macen data kamata sbd sam bata masa shaawan auren baturiya ko balaraba itadai kawai macen gida bahaushiya ko fulani kawai take raayin ya aura din shiyasa bata tirsasahi ba anan amma tabbas suna komawa zata basa umarni da tirsasa aure batareda bata lokaci ba. Bayyana mamakinta yayi tana boye farin cikinta sbd batasan dalilinsa na hakan ba tace "Lafiya dai ko zamu koma Nigeria din? Akwai wata matsalar ne? Akwai abinda yake damunka AZIZ?? kana buqatan adduata ta uwa ne akan wata matsalar??" Shiru ya dan yi kafin yace "No Mama ba matsalar komai, Akwai wani aikin ne dazai sakani komawa kuma zai dauki lokacin da bansan ranar dawowaba, bazan samu nutsuwar barinku anan ni inacan ba shiyasa na yanke zamu koma can din gaba daya, Adduanki kuwa ina baqatanta akoda yaushe Mama sbd samun Nasara akan duk abinda na sakawa gaba." Numfashi mama ta sauke cikin samun nutsuwa tace "Allah ya tsayawa duk wani lamarinka AZIZ, Allah ya Albarkaci duk abinda ka sakawa hannu da gaba, Allah ya Albarkaceka da zuriar da zaka tara yasa inada rabon ganin 'yayanka masu zuwa gaba" Falaq dake amsawa da amin tana jin an ambaci wasu yayan bata fuska tayi taha hararar maman a boye tana cewa "Wannan oldLady din bazata dena cewa Daddyna ya haifi wasu yayanba saikace ni ban ishesaba" Maman data ji abinda Falaq din tace kallanta tayi tace "Bakinki bazai koyi 'daa ba ko? Shiru tayi tana tura baki tareda riqe hannunsa tana qasa qasa da murya tace "Daddy bazaka haifi wasu yayanba bayan ni dan Allah kaji" Dago idanuwansa yayi ya zubawa fuskan falaq din tsawon minti daya kafin ya bude baki cikin nutsuwa zaiyi magana mama ta katsesa sbd tasan zai iya mata alkawarin da bama zai taba yiyuwaba har abada dan kuwa ita nata burin rayuwar shine ganin yayansa a gabanta shine zata samu nutsuwa da farin cikin ganin ya fara tara zuriar kansa daya rasa kowa nasa sbd falaq duk yanda zai sota ba asalin jininsa bace sbd ba shine ya haifeta ba akwai yiyuwar gaba tasan waye asalin mahaifinta dikda basuda wannan niyar sunbarta akan babu me tada maganar waye ya haifeta. Sayd ne ya shigo a shirye sanye da black armanis da glass a fuskansa ya sanar dashi an fidda komai Mota ma is ready. Miqewa yayi bayan ya sakewa mama sallama ya nufi kofa falaq na biye dashi har mota dake bude fahad da zai kaisu Airport ya bude masa yana hango fitowansa. Shigewa yayi aka rufe sayd ma ya shiga gaba fahad ya shiga ya tada motar suka fice gidan. Suna isa Airport basu jimaba suka daga zuwa Italy. #MAMUH #AZIZ AY LIMBA #JANNAH ZAD #ZAADENS #LOVE/HATE STORY #BESTREVENGE #BESTLOVE ZAFAFA BIYAR KALBIM 500 mamuhgee A DUNIYATA 500 Huguma AJIYA A DUHU 500 Billyn Abdul KIRJIN ME HANKALI 500 Miss xoxo Pay at 0022419171 AccessBank Maryam sani gummi Shedan biya 09033181070 Or mtn vtu at 09032345899*_Arewabooks@Mamuhgee_* 45 *ZUZEAM VENTURES* Best APHRODISIAC (kayan mata) 08144015291 Aslm barkanmu da wannan lokaci Ina Mai farin cikin sanar daku cewa Zuzeam ventures takawo maku ingantattun magunguna masu inganci cikin Aminci Muna da kaya kamar haka Mallaka Maganin sanyi Maganin cire tumbiMaganin farin jini Maganin matsiMaganin mata Maganin sa ni’ima da dandano Dulka Amare Set na gyran jiki Set na amarya Tabaje tsumin Gomba Xuma kiba ta hips and Brest Magungunan gyran Brest Magungunan Karin hips Maganin sliming Muna da kaya masu inganci cikin sauki da rahusa Ina wadda keneman mallaka sahihiya quaranty wlh hajiya kixo ga zuzeam ventures xakiji ddin mallaka duk fadin ran ogah duk fadansa wlh sai yyi sanyi 08144015291 Idan maganin mata kikeso akwai Idan gyran jiki kikeso gyran fata gyran Brest magungunan sa kiba da hips DOMIN samunta Kai tsaye kira wannan no 08144015291 DOMIN mgn da ita whatapp 08144015291muna tura kayanmu ko ina cikin iKon allah 🥰👌🏻 Bononza Bononza Tsimin mangoro 1k🥭 Tsimin dabino 1k Gumba ukku balai 700 Gumba aya da nonon rakumi 700 Garin kafi ciccibi 500 Garin bata gaban kishiya 500 Matsin mallaka tada zaune tsaye 2500 Turaren mallaka ba aba mai kishiya 2500 Total kayan 9500 Za a bakisu akan 4200 Kuma mutun goman farko nadakyautar Abun 2k 🗣️🗣️🗣️🗣️🗣️🗣️ ASSALAMU ALAIKUM ALHAMDULILLAH YAN UWA NEW PROMO YA KAMMALA💃🏽💃🏽💃🏽😁😁😁 da 6k dinki ki kwashi kayan 12k hajiyata 💃🏽💃🏽💃🏽😃🙃Kazar gadali ta mallara Rabi 3500 Tsimin gam gam 1500 Ruwan kara zunzurutun dadı😋800 Garin 7in1 1k Gumba 3 balai 500 Gumba kwakwa da dabino 500 Na Infection 1k Garin zunzurutun dadi 1200 Matsin ba a fira d wando 500 Matsin infection mai matse mace gam 500 12k All at 6k https://wa.link/l1gcz8 kedai dannan link dinnan don samun naki ki maza kiyi bucking koda kudinki saida Rabonki ************* Koda suka isa kai tsaye gida aka kaisa sayd kuwa mota ya dauka ya fita zuwa wani aikin wanda a asibitin su dr Nico din dake nan italy aka sadaukar da donor din ismail wanda tini dr Nico ya hada takardun. Sai dare sayd ya dawo bayan komai ya kallama rubuce dan haka washe gari karfe goma suka iso asibitin. Dakin da ismail yake kwance yayi mugun nisa suka nufa babu me shiga sbd yanayinsa da yayi mummunan nauyi dan haka familynsa suna can waiting area suna zaman qunci da damuwa sbd yanda jikin nasa ya koma sun fara cire rai daga rayuwarsa sun zubawa sarautar Allah ido suna jiran hukuncin ubangijin. A natse ya shigo dakin dr Nico na gaba sai Sayd dayake bayansa sai nurse data shigo tana rufe dakin kuma matar Dr Nico dince. Dago fararen idanuwansa yayi da suka sauya yayiwa Dr ismail kallo daya yana daukesu daga kansa sbd jin yake qinsa na tasowa tin daga qasan zuciyarsa yana mamaye dukkanin jininsa. Shiru dakin yayi kafin ya sauke numfashi mara sauti kafin ya tako ahankali ya tsaya akansa Sayd ne ya janyo kujera ya ajiye masa seti da ismail din ya zauna yana dora kafarsa kan daya... Ahankali cikin tsanani na nisan ciwo dr ismail ya bude idanuwansa da sukai jan ciwo ya saukesu akan AZIZ wanda babu kamannin kowa akan fuskansa sai kamannin Ummitah wadda yana kallo ta cika a gabansa... Wasu hawaye ne masu zafi suka gangaro gefen Idanuwansa yana kasa dauke idanuwansa daga AZIZ da shima yake kallansa yana hadiye radadin dayake yagar masa kirji da zuciya. Kasa tsayuwa hawayen dr ismail sukai nadamarsa na bayyanuwa tareda quncin dayake cin ransa, Wani abu me radadi AZIZ ya hadiye kafin ya bude bakinsa ya kalli ismail din da idanuwansa da suka qame yace "Marainiya ce batada uwa batada uba, Cikine a jikinta, Jaririyar 'ya ta haifa, Banda uwa banda uba a duniya itace uwa,uba,'ya,yar wa, Itace tafi mun komai da kowa, Itace kuzarin danake dashi a duniyata, Miji ne da ita da uwar dasuke tsaye kofar dakin suna jiran fitowanta da abinda ta haifa...duka wannan abubuwan kuka take kuka rabata da zuciyar da *fuckin bastard din daya bata ita a cikinku Allah ne ya halitta mata ita kaman yanda ya halitta muku, Meyasa baku cire ta iyayenku kona matanku kun sakawa ita wadda ke buqatan zuciyarba...... Jajir idanuwansa sukai tsananin zafi da ciwon zuciyansa na qaruwa, Tsit dakin sukai babu me magana sai kukan dr ismail din daya fara fidda sauti kadan.. Numfashi AZIZ din ya sauke yana rintse idanuwansa ya hadiye wani dacin zuciya yana controlling kansa cikin sauti me nutsuwa da samun daidaita kansa da sanyi yace "Tirsasa akai,i know you did it coz you don't have a choice, Da saka hannunka aka kashe rai, Kana danasani sbd kayi abinda har abada bazai dena damunka, Ka sani akwai rayuka da dama a duniya irin Ummitah dake neman wata damar ta rayuwa sedai su bazasu iya kashe rai ba, Nema suke sbd Allah batareda cutatar da kowace irin rai ba, Likitoci sun gano ciwonka bazaka taba warkewaba sai wani ikon Allah wanda koda ka warke monsters din da sukai maka wannan abin bazasu taba barin ka rayu ba zasu nemeka duk inda kake su tabbatarda sun kammala aikinsu akanka, A yanayinka yanzu kai kanka kasan bazaka taba moruwa ba idanma ka tashi kenan sbd daga yau na gama biyan sisi a neman lafiyarka zaa maidaka Nigeria su qarasa, Dan haka daka mutu a banza kanada damar gyara kuskurenka ta wani bangaren ta hanyar bawa wani zuciyarka ya rayu, Kodar datake jikinka ma bazata tafi a banza ba zaka iya sadaukarwa wani me tsananin buqata ya rayu, Zaka saka families da dama farin cikin da harsu mutu bazasu dena maka addua da fatar rahama ba sbd sun samu sabuwar rayuwa sbd kai, Karka manta yanda suka kashe Ummitah zasu iya kashe kowama sbd hana sirrin fita...." Hannu ya miqawa Sayd wanda yayi saurin matsowa ya dora masa takardun dasuke hannunsa yana komawa baya. Takardun AZIZ ya budewa ismail yana nuna masa yana cewa "Daga ranar daka bar duniya nayi maka alkawarin daukan nauyin 'yayanka da matarka harsu gama karatu zan bawa mazan aiki matan zan bada dukkanin dukiyar aurensu sbd sadaukarwanka" Kuka ne me sautin da basui tsammani ba yazowa dr ismail din yana rintse idanuwansa cikin tsananin radadin zuciya me zafin gaske. Miqewa AZIZ yayi yana miqawa dr Nico takardun yace "A sanar da familynsa yayi nisa yana son ganinsu da kansa idan harya amince." Juyawa yayi zai fice Dr ismail ya ringa kyafta idanuwansa cikin tsananin kukan da babu sauti ba motsi sai tsananin quncin dayake kokarin saka zuciyarsa neman bugawa. Da sauri dr Nico yayi kansa yana cewa matarsa ta kira familynsa da dr Ayyan. Fita tayi da sauri Sayd kuwa AZIZ daya rintse idanuwansa cikin jin quncinsa na qaruwa kafin ya bude idon ya nufi kofa ya fice batareda ya juyoba sayd yabi bayansa suna barin asibitin gaba daya. Matar dr ismail din kuwa da qaninsa ana kiransu da gudu suka qaraso jikinsu na rawa matarsa kallo daya tai masa ta fasa kuka tana neman shidewa tana qanqame hannunsa. Qaninsa ma tashi hankalinsa yayi idanuwansa sukai jajir. Doctors kuwa kansa suke kokarin rufa amma rikicewa jikinsa yake sake yi... Takardun hannun dr Nico ya qurawa idanuwansa dake neman juyewa yana motsa hannunsa cikin wani irin karfin hali yakeson nunawa matarsa da qanninsa takardun Alamar da yardarsa sedai sam basu lura va sbd tashin hankali. Fiddasu akai da sauri sbd ana buqatan shiga aiki dashi da gaggawa.. Takardun shiga aiki aka basu suka saka hannu aka wuce dashi da gaggawa suna gani matarsa na wani irin kuka shikuwa kanin sunkuyar da kai yayi yana maida hawayensa dake cika idanuwansa duk da sunsan aikin zuciya zaai masa basusan bazai fito da raiba shikenan ya tafi har abada. Ana shiga shigewa da ismail dr Nico da badashi zaayi aikinba ya kira AZIZ ya sanar masa tareda godiyar wanda suka samu donor din dan musulmi ne ma kuma me iyalai dan haka hakan ba qaramin farin ciki da sabuwar rayuwa zai kai a familyn ba. Sayd kuwa take ya fara shirye shiyen komawar familyn dr ismail din sbd yasan shikenan komai ya qare. A lokacinda aka isarwa da familynsa Allah ya karbi ransa yanke jiki matarsa tayi a gurin... Qaninsa ma tashin hankalin ya shiga sedai daman sun riga sun cire rai daga tashinsa dan haka matar aka fara kokarin cetan ranta cikin gaggawa har aka samu ta dawo daidai zuciyarta tai mata wani irin nauyi kukan ma ta nemesa ta rasa sai ajiyar zuciya datake saukewa idanuwanta sunyi jajir. Washe gari anan italy akai masa komai aka rufesa sedai acan gida aka fara zaman karban gaisuwa cikin jimami na baqin cikin rashinsa. Kwanansu biyar a hotel da aka sauya musu sayd ya sakosu jirgi batareda sun taba sanin LIMBA ba ko kammaninsa. Suna dawowa kuka ya dawo sabo a familyn na rashinsa wanda yaransa hudu maza biyu mata biyu suke cikin baqin ciki da qunci. Acan italy kuwa suma a ranar da familyn suka bar qasar kwana daya suka qara suka tattara suka koma gida. Suna dawowa kawai shirin baro kasar suka fara sbd sayd ya kai karshen Wani mahaukacin sabon mansion da aka siya har anyi payment da komai Alh Saad ne da lawyers dinsu a cikin siyansa. Luxuries din da aka zuba gidan saida ya ringa bawa Lawyers din mamaki sbd Yace duk abinda zaa saka yayi daidai da yanayin rayuwar da falaq ta saba ta taso a cikinta dan hakanne ma aka zuba dukiya iya dukiya kaman ba nemanta akeba debowa kawai ake. Securities din kwarai aka dauka aka zuba a gidan bayan an tantancesu tareda masu aiki wainda Latif ne a wannan bangaren yake wannan aikin dan tini ya rufe shago jin ubangijinsu the great AZIZ AY LIMBA zai dawo Nigeria, Shine chief officer na gidan duka maaikanta gidan a karshinsa suke hakama qanansa biyu ya dauko sune drivers na gidan daya hajia mama dayan kuma wanda yafi tsananin kiyayewa da taka tsantsan drivern falaq ne. *********Kusan wata uku suka share suna shirye shiyen kafin suka siya tickets da komai bayan ya nada sabbin presidents da chairmans da directors na companies dinsa dasuke qasar shikuma zai karba na Nigeria din. Babban tarkon daya dana wanda shine sanadin da komai zai fara shine Siye dukkanin hannuwan jarin businesses din sauran companies dasuke aiki da Zaadens batareda saninsu ba sbd a iya bincikensa ya tabbatarda sunada power me karfi, To idan zai kaisu qasa su nema hanyar kabarinsu da kansu to saiya fara rabasu da komai daya bayan, Duk wani abu dasuke so a duniya saiya rabasu dashi akan idonsu...... JANNAH ZAD itace abinda sukeso fiyeda komai kuma suke komai akanta, Tsanar da yake mata batareda ya san waye ita dinba ta gama gauraya dukkanin wani digon jinin dayake yawo a jijiyoyin jikinsa.... Itace zaiyiwa mummunan illan da suna gani batareda sun iya komaiba kafin ya karbe abinda yake nasa daga jikinta yabar musu gangar jikinta. Bazai taba nemansu da kansu yakeson su kawo kansu gurinsa da dukkanin yarda da buqatuwarsu dan haka tashik farko hannuwan jarin daya siye da sunayen Alh Saad da Wasu manyan abokan businesses dinsa ya saka suka ringa janyewa suna cirewa daga business din zaadens wanda cikin qanqanin lokaci arzikinsu yayi wata irin girgizan data sakasu tashi cikin mummunan tashin hankali da tsoro sbd kawai companies dinsu qasa suka fara yi kaman saukan ruwan jiki...... Hakama kusan manyan ma'aikatansu da suke ji dasu take suka ringa ajiye aiki bayan sun satar musu manyan kudaden dasuka qarasa Jijjigasu kuma sata irin tsaftatacciya da babu inda suka bar evidence ko record na fitar kudaden gaske. Neman zaucewa sukeyi take suka tashi tsaye da neman hanyar tsayar da wannan iftilain kwatsam daddy mahmoud dayake can qasar daga fita aka kira ya samu stroke. Bp din Dzad daya dena tashi tinda Jannah ta samu lafiya ne ya tashi hankalinsu yafara tashi sedai sam basu bari duniya tasan suna yin qasa ba. Sbd gudin raba hankalinsu biyu a yanzu da suke cikin crisis dawo da daddy mahmoud Nigeria akai suka hade mansion daya ana jinyarsa a gida kawai aka dauki manyan doctors dake zuwa dubasa kullum. A ranar da aka dawo da mahmoud Nigeria jirgi daya ne ya saukesu a Nigeria da LIMBAS family wainda motaci suka daukesu zuwa LIMBAS mansion. #MAMUH ##BESTSTORY #KALBIM ZAFAFA BIYAR KALBIM 500 mamuhgee A DUNIYATA 500 Huguma AJIYA A DUHU 500 Billyn Abdul KIRJIN ME HANKALI 500 Miss xoxo Pay at 0022419171 AccessBank Maryam sani gummi Shedan biya 09033181070 Or mtn vtu at 09032345899*_Arewabooks@Mamuhgee_* 46 *ZUZEAM VENTURES* Best APHRODISIAC (kayan mata) 08144015291 Aslm barkanmu da wannan lokaci Ina Mai farin cikin sanar daku cewa Zuzeam ventures takawo maku ingantattun magunguna masu inganci cikin Aminci Muna da kaya kamar haka Mallaka Maganin sanyi Maganin cire tumbiMaganin farin jini Maganin matsiMaganin mata Maganin sa ni’ima da dandano Dulka Amare Set na gyran jiki Set na amarya Tabaje tsumin Gomba Xuma kiba ta hips and Brest Magungunan gyran Brest Magungunan Karin hips Maganin sliming Muna da kaya masu inganci cikin sauki da rahusa Ina wadda keneman mallaka sahihiya quaranty wlh hajiya kixo ga zuzeam ventures xakiji ddin mallaka duk fadin ran ogah duk fadansa wlh sai yyi sanyi 08144015291 Idan maganin mata kikeso akwai Idan gyran jiki kikeso gyran fata gyran Brest magungunan sa kiba da hips DOMIN samunta Kai tsaye kira wannan no 08144015291 DOMIN mgn da ita whatapp 08144015291muna tura kayanmu ko ina cikin iKon allah 🥰👌🏻 Bononza Bononza Tsimin mangoro 1k🥭 Tsimin dabino 1k Gumba ukku balai 700 Gumba aya da nonon rakumi 700 Garin kafi ciccibi 500 Garin bata gaban kishiya 500 Matsin mallaka tada zaune tsaye 2500 Turaren mallaka ba aba mai kishiya 2500 Total kayan 9500 Za a bakisu akan 4200 Kuma mutun goman farko nadakyautar Abun 2k 🗣️🗣️🗣️🗣️🗣️🗣️ ASSALAMU ALAIKUM ALHAMDULILLAH YAN UWA NEW PROMO YA KAMMALA💃🏽💃🏽💃🏽😁😁😁 da 6k dinki ki kwashi kayan 12k hajiyata 💃🏽💃🏽💃🏽😃🙃Kazar gadali ta mallara Rabi 3500 Tsimin gam gam 1500 Ruwan kara zunzurutun dadı😋800 Garin 7in1 1k Gumba 3 balai 500 Gumba kwakwa da dabino 500 Na Infection 1k Garin zunzurutun dadi 1200 Matsin ba a fira d wando 500 Matsin infection mai matse mace gam 500 12k All at 6k https://wa.link/l1gcz8 kedai dannan link dinnan don samun naki ki maza kiyi bucking koda kudinki saida Rabonki ************ Maheer dayafi mintina arbain yana waya daya a tsaye cikin office dinsu dayake gida, Dad ne zaune shikuma yana duba tarin reports na acct histories na duka companies dinsu yana ganin yanda suka sauka qasa sosai a lokaci daya kamar aikin asiri, Cikeda mamaki da tsananin bacin rai da baqin ciki yana duba yakardun duka partnerships masu da aka janye aka barsu. Ammar dayake can yana nasa wayoyin da binciken cikin tsananin baqin ciki da mamaki babu wani bayani ko daya daya samu na wanda ya siye duka hannun jarin dayake kamfaninsu dan haka ya shigo office din fuskansa ba walwal ya tsaya gaban dad daya dago idanuwansa jajir ya kallesa yace "Me aka samo?? Ka gano ko waye? Girgiza kai yayi zuciyarsa na daukan zafi yace "No dad, Ko waye ba qaramin Monster bane sedai ko waye shi zamu ganosa sbd he's playing with the wrong people, Ya taba wutan da zata konasa ko garwashinsa baa samuba" Maheer daya gama waya cikin damuwa ya kalli Ammar din kafin ya kalli dad yace "Duk yanda nayi sunriga sun siyar masa kuma baama sansama bare mu fuskancesa da kanmu yasan da waye yake, Sune a tsaye akan janyewan kwata kwata duk tsawon kwanakin nan babu alamar ko hanya daya da zamu gane waye a bayansu, Hakama muna cikin tsananin stock market crash sbd komai na sauka rapidly da dole mu dakatar da komai for now mu tsayar da marketing da duk wani aiki a companies namu aje break kafin a gano kan matsalar coz idan aka tafi a hakan babu bata lokaci zamu iya qarasa rasa komai so a tsayar da komai" Dagowa Dad yayi ya kallesa idanuwansa na jajir sbd dakatar da komai na nufin zasu rufe komai sai sun daidaita.. Ammar ma cikin tsananin kasa yadda da hakan ya kalli Maheer yace "No,we cant do that,tayaya kake tinanin zamu dakatar da komai namu? Katsesa Maheer yayi cikin damuwa da cewa "Dole sai anyi hakan idan har munason cigaba da amsa sunanmu da riqe power dinmu idan ba haka zamuyi zubewanda zamu jima bamu dawoba duk da munada tarin dukiyar da bazai taba iya talautamuba amma karku manta arzikinmu bai taba girgiza ba sai yanzu, Ya girgiza mana arziki da karfi sbd a cikin kaso biyar mun rasa kaso uku, To idan bamu tsaya ba muka sauya taku zamu qara zubewan da kaso daya bazai riqemu a rayuwar da muka saba da ita hakama duniya da sauran business partners namu zasu fahimci mun rasa power da muke da ita wadda har abada bazamu bari a san da hakanba dan haka komai zai zama iya sirrin cikin familyn ne,babu wanda zaisan mun girgiza" Dad dayakejin zuciyarsa na tafarfasa bude idanuwansa yayi ya kalli Maheer yace "Ka tabbatarda ancigaba da tsananta bin sirrinsu an nemo mana wanda yayi backing komai, inason a fasa kansa da bullet sbd indai yana duniyar zai ringa alfahari daya girgiza Zadeens hakama ya taba wainda baa tabawa dan haka duk tsanani inason a nemosa dan yayi danasanin wannan abinda yayi" Gyada kai Maheer yayi Ammar ma gyada kan yayi yana tinanin tayaya zasu ajiye komai suyi me to?? Zaunawa sukai sunayin shiru sbd kosu Mimi da Jannah basusan meyake faruwaba iya mazan abin ya tsaya.. Waya Maheer ya fidda tareda saka kiran Saleem daya kusan zarewa shikuma akan Sabon business dinsu kamfanin motoci da a yanzu shine babban hope dinsu dazai dawo musu sa percents din da suka rasa gashi basu gama bayyanarwa da duniya kamfanin ba dan haka wanda yake wasa dasu bai saniba hakama AY LIMBA da suka fahimci zafin kansa da kuma saar da ake fada yanada ita dole dashi zasuyi business. Saleem daya shigo da laptop dinsa da takardu a hannunsa ajiyewa yayi ya kalli dad din wanda zuciyarsa ke ciwo Ammar da idanuwansa sukai jajir Maheer ya bude baki cikin rashin mafita bayan wannan yace "Dad,LIMBA ne abinda muke buqata a business dinmu yanzu sbd sabon kamfanin nan shine zamu daga ya bamu abinda mikeso, Muna buqatan aiki dashi gaba dayanmu a yanzu ba Saleem ba" Dad din bayanan komai AZIZ AY LIMBA ya karba takardun yana karantawa tareda tarin nasarori da asalin dukiyar dayake da ita hakama ga connections na manyan mutanen da baima taba tunanin matashi kamarsa ba suna hulda dashi wanda a taqaice Abokin manya ne shi kansa ya wuce ace shine yake neman wani sedai a nemesa kaman su kenan, Hanyoyin bullewa ya gano da Yawa ta hanyar AZIZ din dan haka ya ajiye takardun yana sauke ajiyar ya dago ya kalli Maheer yace "No da kaina zan business dashi dan haka ina buqatan haduwa dashi, Muna buqatansa a matsayin friend na zaadens, Damu ya kamata yayi hulda fiyeda kowa dan haka kowa ya tabbbatarda hakan ta faru na samun kusancinsa damu" Maheer jin wani irin sanyi yayi yana sauke ajiyar zuciya a bayyane sbd tabbas suna buqatan self made billionaire me zafin kai kamar AZIZ AY LIMBA sbd su samu saarsa, Saleem kuwa dayake kaunar kasancewa da AZIZ LIMBA ba tin yanzu ba jin yayi zuciyarsa tayi sanyi farin ciki na cikesa sbd kaunarsa yake har ransa. Ammar kuwa jin yayi zuciyarsa na shiga yanayin daya kasa gane farin ciki ne,tsoro ne,fargaba ne ko baqin cikin Zasu kusancesa da kansu batareda yazo garesu ba sbd power dinsu da matsayinsu hakama jin yayi tsananin kishinsa akan zamansa selfmade billionaire sabaninsu da tasowa sukai a cikinta ta iyayensu ce ta gado bawai sune suka tsayu suka samarwa kansu sunan kamarsa ba... Saleem ne kawai me raayin kirkirawan kansa suna ya gina dukiyarsa da kansa dan yayi bugun gaba da shine ya gina kansa bawai iya alfahari da dukiyar familynsa ba dan hakanne ma yake shaawar AZIZ AY LIMBA wanda akace baida uba a maraya ya taso daga shi sai mahaifiyarsa da 'yarsa daya tak wadda babu wanda ya taba ganin mahaifiyarta dan haka babu wanda yasan rasuwa tai kokuwa rabuwa sukai haryau wannan sirrin shine babu wanda ya sani akansa. Da wannan shawaran da suka tsayar suka samu sassauci da damar dawowa hayyacinsu suka fito meeting din da kullum sai sunyisa dan neman mafita. Kowannensu na fitowa kai tsaye Bedroom dinsa ya nufa dan samun nutsuwar da suka rasa ta kwanakin. Anny da hankalinta ya fara tashi ganin suna neman durqushewa jin an samu mafita daga bakin Maheer din samun kanta tayi da jin dadi da dawowa hayyacinta duk da tasan suna zubewa qasar zasu bari su koma Greece inda suka fito su dasa sabuwar rayuwar rufin asiri sbd girman kansu bazai bari su zauna anaba ana musu kallan sun rage karfin dasuke dashi kwata kwata. ********washe gari gaba daya familyn suna dining room suna breakfast harda daddy mahmoud dayake zaune a wheelchair dinsa sedai baya iya cin komai se abinci me ruwa duk da yafara samun sauki, Jannah ce ta shigo dining room din a natse sanye da riga da wando daya lafe a cinyoyinta sai rigar Cardigan da qaramar scarf akanta. Ammar ne tareda ita gefenta qamshinsa da nata ya cakude yana fita a tare yana bada wani kalar qamshin me dan dadi. Mimi kallonsu tai tanajin ita dai batada nutsuwa idan ba aurensu akaiba duk da tasan yanzu ba lokacin maganar aurensu bane sbd lura kwanakin a kwai matsalar datake faruwa ta aiki duk da baa sanar mata ba ta fahimta kuma itama bata saka baki ba addua kawai tai musu. Zaunawa sukai bayan sun gaida kowa suka fara breakfast din. Wayar Maheer ce tai ringing yana dubawa yaga pa dinsa ne Ajiye wayar yai batareda ya dauka ba saida ya gama breakfast dinsa ya dauki tissue ya goge bakinsa yana miqewa ya saka kiransa. Cikin girmmawa deen pa din nasa yace "Goodmorning Boss" Amsawa yayi yana zaunawa a kan sofa yace "Any news??? "AY LIMBA yana Nigeria gaba daya ya dawo tareda familynsa a cikin satin daya gabata" Dan tashi daga jinginar da yayi maheer yayi yana cewa "A ina?? "A abuja boss" Wani numfashin farin ciki da samun kwanciyar hankali Maheer din ya sake yana cewa "Kaje in person kai magana da Personal person nasa Muna neman gayyatarsa na welcoming nasa kafin maganar business gaba" "Yes an gama boss" Kashe wayarsa yayi bayan yace a nemo contact na LIMBA din a gurin SAYD. Dad na zaunawa palon Maheer din ya sanar dashi LIMBA na Nigeria cikin samun nutsuwa. Shi kansa dad zancen ya sake sakasa cikin kwanciyar hankali sbd da kansa yakeson kulla Kyakkyawar alaqa me karfin gaske da LIMBA sbd baya wasa da billionaires dan haka da kansa zai jagoranci neman kusanci da Limban sbd kada ma su kawo matsala ko daya su 'yayan nasa. *********Sayd dayake jiran kiran Zaadens din tin ranar da suka dawo Nigeria se yau ya samu kiran daga garesu dan haka cikin rashin basu mahimmanci a natse ya gama sauraron bayanin Deen kafin ya basu damar contacting Limba din kai tsaye wanda Maheer ne ya kira AZIZ da kansa sedai bai daga ba sbd baimasan numbern ba sai kusan bayan kwana biyu daya sake kira kafin Ya daga cikeda iko da nutsuwa da izzansa data saka Maheer jin kishinsa me tsanani ya rufesa sedai kuma yana tsananin son kasancewansu dashi dan haka cikin tasa class din da wayewa tareda dukiya daya taso cikinta da hutu suka gaisa ya gabatar masa da kansa. Wani irin yanayi me daci ne ya dan tasowa AZIZ din yanajin saukan muryan Maheer din kamar wani yankan rezan dayake yanka zuciyarsa sbd bai taba tinanin zai iya sauraronsu da kunnuwansa masu tsafta ba. Bude kyawawan idanuwansa da ya dan rufe yana cigaba da sauraron Maheer din wanda ya nuna masa sakewa. A natse cikin kwanciyar yake dan magana kafin ya amince da gayyatarsu na haduwa bayan yace zai duba proposal nasu da suka turawa sayd insha Allah zaizo da approval nasa na hada business din. Sallama sukai Maheer na cikin farin ciki da samun cikar burinsu dan haka suka fara shirin tarbonsa a Zad mansion. ##MAMUH ZAFAFA BIYAR KALBIM 500 mamuhgee A DUNIYATA 500 Huguma AJIYA A DUHU 500 Billyn Abdul KIRJIN ME HANKALI 500 Miss xoxo Pay at 0022419171 AccessBank Maryam sani gummi Shedan biya 09033181070 Or mtn vtu at 09032345899*_Arewabooks@Mamuhgee_* 47 *ZUZEAM VENTURES* Best APHRODISIAC (kayan mata) 08144015291 Aslm barkanmu da wannan lokaci Ina Mai farin cikin sanar daku cewa Zuzeam ventures takawo maku ingantattun magunguna masu inganci cikin Aminci Muna da kaya kamar haka Mallaka Maganin sanyi Maganin cire tumbiMaganin farin jini Maganin matsiMaganin mata Maganin sa ni’ima da dandano Dulka Amare Set na gyran jiki Set na amarya Tabaje tsumin Gomba Xuma kiba ta hips and Brest Magungunan gyran Brest Magungunan Karin hips Maganin sliming Muna da kaya masu inganci cikin sauki da rahusa Ina wadda keneman mallaka sahihiya quaranty wlh hajiya kixo ga zuzeam ventures xakiji ddin mallaka duk fadin ran ogah duk fadansa wlh sai yyi sanyi 08144015291 Idan maganin mata kikeso akwai Idan gyran jiki kikeso gyran fata gyran Brest magungunan sa kiba da hips DOMIN samunta Kai tsaye kira wannan no 08144015291 DOMIN mgn da ita whatapp 08144015291muna tura kayanmu ko ina cikin iKon allah 🥰👌🏻 Bononza Bononza Tsimin mangoro 1k🥭 Tsimin dabino 1k Gumba ukku balai 700 Gumba aya da nonon rakumi 700 Garin kafi ciccibi 500 Garin bata gaban kishiya 500 Matsin mallaka tada zaune tsaye 2500 Turaren mallaka ba aba mai kishiya 2500 Total kayan 9500 Za a bakisu akan 4200 Kuma mutun goman farko nadakyautar Abun 2k 🗣️🗣️🗣️🗣️🗣️🗣️ ASSALAMU ALAIKUM ALHAMDULILLAH YAN UWA NEW PROMO YA KAMMALA💃🏽💃🏽💃🏽😁😁😁 da 6k dinki ki kwashi kayan 12k hajiyata 💃🏽💃🏽💃🏽😃🙃Kazar gadali ta mallara Rabi 3500 Tsimin gam gam 1500 Ruwan kara zunzurutun dadı😋800 Garin 7in1 1k Gumba 3 balai 500 Gumba kwakwa da dabino 500 Na Infection 1k Garin zunzurutun dadi 1200 Matsin ba a fira d wando 500 Matsin infection mai matse mace gam 500 12k All at 6k https://wa.link/l1gcz8 kedai dannan link dinnan don samun naki ki maza kiyi bucking koda kudinki saida Rabonki ************ A bangaren LIMBAs komai yana tafiya a familyn daidai sbd falaq bata samu damuwa ko jin rashin dadin qasarba sbd bata taba zuwaba tinda aka tafi da ita gana Nigeria dan haka kamar wannan ne zuwanta na farko bayan data barta dan haka suke tinanin zata iya shiga damuwa da rigimar batason nan din amma kuma a nata bangaren Nigeria din ta zama best gurin da zatai rayuwa me dadi sbd daddynta zai kasance dasu ba yawan tafiye tafiye dan haka hankalinta yake kwance sbd tana tareda familynta duka hakama yanayin duniyar dake cikin gidan yasakata batajin wani banbanci da qasar da suka baro dan haka takejin dadinta kawai hankalinta kwance. Kwanciyar hankalinta da walwalwanta ya saka gabaki daya gidan suma suke cikin walwala da kwanciyar hankali da farin cikin komai yana tafiya daidai gashi daga mama har Fiddausi suna cikin farin cikin dawowan dan gashi sam bai fadawa mama abinda akaiwa Ummitah ba dan kada ya sakata quncinda baida magani dan haka suke cikin walwalansu gidan. Baba alhassan ma ya taho yana abujan saiya huta yanda ya kamata zai koma gida dan haka sosai gidan ya zama cikin walwala. Falaq sosai suke fita yawo da Latif da Fiddausi sbd taga gari da yawon shopping. Ya karba gayyatarsu ne sbd bazai bari su sukawo masa ziyarar ba dan bayason abinda zai kawosu cikin gidansa da iyalinsa dan haka zai dira a nasu empire din da kansa. ****A cikin qanqanin lokaci ya kasance suna yawan waya dashi harma dashi Dzad din dakansa dan haka ya fara sakar musu hanyoyin businesses da suke buqata sbd su sake jikinsu sosai dashi. A ranar daya shirya ziyartar familyn da nasa familyn sbd yanda suke son haduwar familyn nasu... Cikin nutsuwa dukkani familynsa suka shirya suka fito banda Baba alhassan da hutu kawai akeson yayi. Lafiyayyar RR ce da beymach Baqaqe suna daukan ido suka kawosu mansion din Zaadens da ake jiransu cikin Kyakkyawan tarba wanda suma lafiyayyun motocine a jere harabar gidan dan dukkanin wanda yake gidan yana motan datake amsa sunanta mota shi dad dinma kusan uku ne dashi Maheer ma biyu dashi sauran daddaya ne sbd basason mota da yawa. Securities din gidan da sauri suka budewa motocinsu gate suka sako kai a cikin gidan sayd na kallan Zaadins din dake fitowa daya bayan daya cikin iko da suke murzawa dan tarban AZIZ LIMBA da basusan balai da masifar rayuwarsu ce suka fito tarba da hannu bibbiyu ba. AZIZ kuwa idanuwansa ya tsayar akan Dzad dayake fitowa sanyeda kayan alfarma cikin dattako da nutsuwa ta ilimi daya ratsashi da dukiya amma zuciya duk tsatsa sedai yayi masa alkawarin kankare tsatsar zuciyarsa da abinda yafi tsatsan muni. Parking aka latif ya fito daga mazaunin driver yana budewa mama mota, Sayd kuwa AZIZ ya budewa sayar motar. Fitowa qafafunsa ya ziro a natse yana fitowa sanyeda navy blue wata tsadaddiyar cashmere data fidda tsananin haske da kyan fatarsa da hutu ne kawai a bayyane koina na aji. Gabaki daya sun Maheer zuba masa idanuwansu sikai aura dinsa na cike idanuwansu da kuma asalin nutsuwa da steez dinsa. Hannu ya miqa a natse ya budewa Falaq mota wadda a duniya ita kadaice yakewa hakan. Kallan wanda aka budewa mota sukai suna jiran ganin ko matarsa ce suka ga Yarinya qarama ce wadda kai tsaye suka fahimci itace 'yar da babu abinda yakaita mahimmanci kaf rayuwarsa. Fuskanta dauke yake da murmushi koda ta fito sanye da doguwar riga lilac da mini hijab dinta. Hannunsa ta kama cmda sauri cikin nata tana murnan sunzo baqon guri sbd tanason shiga mutane sosai sbd ta taso a killace. Mama da Fiddausi ma cikin walwala suke ganin daga karshe ya yadda zasuyi muamala da mutane sosai tinda gasu a cikin wani familyn sun kawo ziyara wanda sai wanda ya yadda yayi kusanci dasu yake hakan. Cikeda sakewa da farin ciki tareda bayyanarda shaquwa Maheer ya miqa masa hannu yana cewa "Welcome to zaadens LIMBA" Dagowa yayi yana miqa masa hannunsa tareda sakin wani lafiyayyan murmushin daya saka Zuciyar Jannah data sako kai dauke wuta cak tana kallansa idanuwanta na cikowa da hawayen da batasan na meneneba batareda ta qara taku ko daya ba... Anny data sako kai tareda jannah din itama wutar ta dauke tana zubawa masa dukkanin idanuwanta zuciyarta na ambatar sunan Allah. Dad cikin sakewa da bayyanarda farin cikin samunsa a gidansu yau din ya miqa masa hannu shika ya miqa masa yana cewa "The pleasure is mine" Ammar ma cikin danne abinda yakeji ya sake fuska cikin nuna farin cikinnsa yai masa welcome. Saleem kuwa da farin cikin ganin AZIZ din yake tin daga zuciyarsa murnan haduwansu ya bayyana masa suna qarasawa ciki. Mimi datake fitowa daga dining room da aka gama hadawa da farin ciki ta tarbi su mama tana musu sannu da zuwa. Itama maman cikin sakin fuska take amsawa. Anny juyowa tayi ta kalli jannah data kasa motsawa jikinta a sanyaye musamman daya rabata ya wuce ciki batareda ya lura da ita dinba a karo na biyi kenan yana mata hakan yabarta da kamshinsa daya saka kanta cakewa tana kasa dauke idanuwanta akansa. Anny zuba mata idanuwanta tayi tana nazartanta batareda tace komaiba.... Me yake shirin faruwa? Me jannah ke tinani? Cabdijam" tafada a fili tana shiga lissafin da idan har hakanne to wlh saita tabbatarda hakan ya faru sbd a yanzu da AZIZ LIMBA yake gabansu to iya business dashi ba shine kadai zai fiddasu ba suna buqatan hada family dashi ta hakan ne zasu shiga dukiyarsa su juya a cikinta su samesa yanda sukeso, Dan Maheer na buqatan sanin hakan indai neman mafita suke kuma a saukake Lamarin zaizo indai Jannah ta kamu da tsananin son AZIZ din dan haka tayi Alqawarin sakawa jannah din tsananin son AZIZ LIMBA batareda saninta ba sbd kamuwa da sonsa kawai zaisaka familyn su hana aurenta da Ammar su aura mata wanda takeso... Wani Murmushi ta sake tana kallan jannah din cikin tausayi dan babu alamar Akwai mace ma rayuwar LIMBA bare soyayya... Taba jannah din tayi ahankali tana cewa "Cewa Jan muje ko" Ciki suka nufo Anny din na gaba Jannah na bayanta a natse. Dad ne dasuke zaune suna magana kowa a cikin wayewa da arziki daya gama hudasu ya kalli jannah yana miqa mata hannu yacewa AZIZ "Meet the princess of d family JANNAH ZAD my daughter" Dago Fararen idanuwansa yayi an natse ya saukar akanta daidai itama ta dago tana kallansa bayan ta kama hannun dad dinta ta zauna kusa dashi. Fuskanta yayiwa kallan Minti daya yanajin wata wuta me zafin gaske tana cin zuciyarsa, Kallanta kadai qona rahamar idanuwansa yakeyi... Ahankali cikin nutsuwa ya gangaro da idanuwansa setin zuciyarta dake bugawa ahankali tana dauke idanuwanta daga kallansa sbd yanda idanuwansa ke karya kuzarinta zazzabi na neman rufeta. Kirjinta ya zubawa ido yana karantar yanda bugun zuciyarta ke bayyana akan rigar data kwanta jikinta... Falaq dake gefensa zaune ganin yanda gurin yayi shiru ta kwantar da fuskanta gefen jikin daddynta itama tana kallan jannah wadda ta kasa bude baki ta gaidasa. Maheer ne yake fara bayanin inda jannah din tai zama da karatunta. Sai alokacin jannah ta bude baki a hankali ta gaidasa sedai dauke idanuwansa yayi daga bangaren datake yana maida kan dad suna magana batarda ya amsaba sbd jin muryanta tamkar xuban ruwan dalma a kunnensa, Tsana me karfin gaske da babu sirki ko sassauci a cikinta yakewa komai daya danganceta, Jinsa a cikinsu tamkar a tsakiyar tekun wuta yake jinsa sbd tsanar dayake musu ba yar qarama bace, Qi da fushin dayakeji yana cin zuciyarsa baya misaltuwa amma a hakan ya daure yana zaune a cikinsu sbd a cikakkiyar sabon binciken da akai masa akansu bazai taba kaisu qasa ba ya lalata gabaki daya asali da sunansu da rayuwarsu gaba dayaba saiya shiga cikinsu, To amma kuma abinda ya fahimta sabo a cikinsu dinma shine Jannah Zad itace kadai abinda zasu rasa su tashi aiki gaba dayansu.... Miqewa jannah din tayi tareda bawa falaq hannu tana nuna mata kofa da idanuwansa tace "Muje gurinsu Mimi ta gaisa da???? Cikin kai tsayenta data saba sbd gatan da yayi mata yawa itama tace "Falaq Aziz" Murmushi me kyau jannah din ta sauke tana kama hannunta suka fice tana cewa "Falaq" "No i said falaq Aziz not Falaq okay?" Dariya jannah tayi tana qarasa janta zuwa palon Mimi dasu mama sukecan fira ta barke kaman sun saba. #MAMUH #KALBIM ZAFAFA BIYAR KALBIM 500 mamuhgee A DUNIYATA 500 Huguma AJIYA A DUHU 500 Billyn Abdul KIRJIN ME HANKALI 500 Miss xoxo Pay at 0022419171 AccessBank Maryam sani gummi Shedan biya 09033181070 Or mtn vtu at 09032345899*_Arewabooks@Mamuhgee_* 48 *ZUZEAM VENTURES* Best APHRODISIAC (kayan mata) 08144015291 Aslm barkanmu da wannan lokaci Ina Mai farin cikin sanar daku cewa Zuzeam ventures takawo maku ingantattun magunguna masu inganci cikin Aminci Muna da kaya kamar haka Mallaka Maganin sanyi Maganin cire tumbiMaganin farin jini Maganin matsiMaganin mata Maganin sa ni’ima da dandano Dulka Amare Set na gyran jiki Set na amarya Tabaje tsumin Gomba Xuma kiba ta hips and Brest Magungunan gyran Brest Magungunan Karin hips Maganin sliming Muna da kaya masu inganci cikin sauki da rahusa Ina wadda keneman mallaka sahihiya quaranty wlh hajiya kixo ga zuzeam ventures xakiji ddin mallaka duk fadin ran ogah duk fadansa wlh sai yyi sanyi 08144015291 Idan maganin mata kikeso akwai Idan gyran jiki kikeso gyran fata gyran Brest magungunan sa kiba da hips DOMIN samunta Kai tsaye kira wannan no 08144015291 DOMIN mgn da ita whatapp 08144015291muna tura kayanmu ko ina cikin iKon allah 🥰👌🏻 Bononza Bononza Tsimin mangoro 1k🥭 Tsimin dabino 1k Gumba ukku balai 700 Gumba aya da nonon rakumi 700 Garin kafi ciccibi 500 Garin bata gaban kishiya 500 Matsin mallaka tada zaune tsaye 2500 Turaren mallaka ba aba mai kishiya 2500 Total kayan 9500 Za a bakisu akan 4200 Kuma mutun goman farko nadakyautar Abun 2k 🗣️🗣️🗣️🗣️🗣️🗣️ ASSALAMU ALAIKUM ALHAMDULILLAH YAN UWA NEW PROMO YA KAMMALA💃🏽💃🏽💃🏽😁😁😁 da 6k dinki ki kwashi kayan 12k hajiyata 💃🏽💃🏽💃🏽😃🙃Kazar gadali ta mallara Rabi 3500 Tsimin gam gam 1500 Ruwan kara zunzurutun dadı😋800 Garin 7in1 1k Gumba 3 balai 500 Gumba kwakwa da dabino 500 Na Infection 1k Garin zunzurutun dadi 1200 Matsin ba a fira d wando 500 Matsin infection mai matse mace gam 500 12k All at 6k https://wa.link/l1gcz8 kedai dannan link dinnan don samun naki ki maza kiyi bucking koda kudinki saida Rabonki *********** Mama da sai alokacin ta lura da Jannah ta kuma ganeta cikeda kulawa da sakewa tace "Ah ah beauty din Falaq ce wannan ai" Falaq dake gefen jannah din barin gefenta tayi da sauri tana qarasawa gurin mama ta zauna tana bata fuska tace "No,yaushe na fada hakan? She's not my beauty,i dont even like her sbd ta taba cewa wani yafi daddyna and nikima ban hada Bestyna da kowa ba" Mimi dake kallan Falaq din cikeda kauna da kulawa dariya me nutsuwa takeyi kafin tace "Idan kuwa hakan jannah ta fada tabbas she's not your beauty sbd daddynki yafi kowa ko?? Gyada kai tayi tana hararar Fiddausi dake boye dariyarta sbd sai yanzu itama ta gane jannah din kuma tasan mama ta kwafsawa Falaq sbd ta zubar mata da class. Jannah murmushi takeyi tana kallan falaq din cikeda kaunarta datake jin tana gauraya zuciyarta cikin sanyi dan haka qarasowa tayi ta zauna kusa da falaq din tana miqa mata hannu sbd ta fahimta mama ta bude mata aiki ne dan haka tace "I'm sorry for saying that amma ai a baya ne kafin na gans...." Kasa qarasawa tayi tana cewa "Bazan qara fadan hakan" Juyowa Falaq tayi tana kallan Kyakkyawan fuskanta tace "Kin yadda babu handsome kamarsa?? Zubawa falaq din idanuwanta tayi tana kallan kyan kamanninta ta kasa fadan hakan sbd idon Mimi dayake kanta hakama Anny. Basar da zancen taso yi falaq tace "Haryanzu baki yadda ba kenan??? Bata fuska tai tana kokarin matsawa daga kusa da ita jannah din ta riqeta tan cewa "Na yadda mana" Murmushi falaq din ta sauke tana cewa "Duk da haka ban hakura ba duka gaskia amma dai na dan sauko zamu iya gaisawa yanzu" Hannu jannah ta miqa mata tana biyewa shirmen tace "Friends?? Kaman falaq bazata bada hannunba ta miqa mata tana murmushi. Fiddausi cikin bayyanarda murnanta tace "Daga karshe Falaq Aziz yau tayi qawa a tayamu murna" Mama dariya tayi tanawa jannah din kallan kauna Itama Mimi murmushin take tana dawo da kallanta kan mama suna cigaba da magana. Jannah kama hannun Falaq tayi suka bar palon tana cewa Fiddausi ta biyosu. Bedroom dinta suka nufa Suna shiga dakin akan hoton Ammar dake gefen gadon dakin idanuwan Falaq suka sauka ta zake guntun tsoki mara sauti tana cewa "Yayi kama da namijin witch ma" Fiddausi data jita hoton ta kalla tana mamakin zancen da dariya lokaci daya. Jannah kuwa zaunar da ita tayi ta kira kitchen aka kawo musu tarin kayan zaqi dasu chocolates wanda kusan taste dinsu daya da falaq wadda aka hana cin chocolates da wasu abubuwan sbd kiba takeyi. Fiddausi kuwa jannah din take kallo wanda komai nata yake a natse cikin burgewa da tsari. Falaq kuwa an samu abinda akeso sakewa tayi tana ciye ciye suna kallan abubuwa a ipad din jannah din suna dariya kaman sun saba. A can palon Dzad kuwa fira ce ta business take wakana a tsakaninsu cikin sakewa da ilimi suna bayyanar masa da irin nasarorinsu na rayuwa da successful businesses dasuka diba shekaru suna gudanarwa. Mayen murmushi akan fuskansa batareda yacika bayanin tasa nasararba tasu yake saurara yana mamakin irin yanda a zantukansu yake karantar halayen kowannesu da fahimtarsu daya bayan daya yana kokarin fahimtar waye likita a cikinsu amma dayake sunada wani irin riqe sirrinsu da kiyayewa sam babu wata alamar da zata ganar dashi komai. Abu dayane yake sake fahimta a kowannensu shine zasu iya komai akan kaunar dasukewa junansa, Suna tsananin kaunar junansu babu shakkar hakan tabbas, Amma kuma jannah din dai itace tamkar zuciyar kowanne Zaaden, Itace basa hadata da komai ko a gurin zance, Sun nuna,sun fada kuma idanuwansu da komai nasu ya nuna hakan sbd sunason yasan da hakan sbd kiyayewa da tsaro dan yasan ko rai zasu iya dauka akanta. Wani shegen murmushi ya sake a lokacinda ya fahimci abinda suke nufi da nuna masa hakan a cikin kwanciyar hankali da wayewa batareda damuwar komaiba. A natse ya dan yi baya yana jingina da jikin sofan dayake da muryansa mai cikeda nutsatsiyar wayewansa yace "Inada nawa princesses din guda biyu da ba rai kadai zan iya dauka akansu ba rayuka zan lalata ba adadi akansu, Dayan is no more dayar kuma is my little besty da kuka gani Falaq Aziz so i understand coz atleast we have this in common" Cikin walwala suka fahimci shima tasa 'yar ce weakness dinsa dan haka kaman yanda ya fada suma sun fahimta, Ammar ne wanda kwata kwata ya kasa walwala yanda ya kamata sedai lura da kaman ya shima zai iya komai akan abinda yakeso kamar yarsa dan haka yaji atlast yanada abinda ya birgesa dashi dan haka ya dan fara sakewa yana shiga firar wadda Maheer da dad tini suka sake jiki suka koma tamkar sunyi shekaru dashi sbd komai nasa yayi musu dari bisa dari tin daga kan ilimin daya mugun ratsashi da attitude nasa da tsagwaron zamansa genius dan ga kwanciyar hankali irin ta wadata ba hayaniya dan haka sunga guri sukam. Dinner sukai gabaki dayansu a dining room bayan sunyi sallan magrib. Falaq datake dakin Jannah tin dazu Sunyi sallan magrib tare suka fito cin abincin falaq na jin dadin yawon da jannah tai mata alkawarin zata kaita taga gurare suka nufo dakin cin abincin. Mama da Mimi ma da suke dakin Mimin sunyo sallan dining suka nufo suna zaunawa saleem ya shigo ya zauna saiga jannah da falaq din suma sun shigo saiga Anny sanye cikin wani kayan daban tayi wanka ta sauya. Su Dad ne zuka shigo dining room din AZIZ din na gefen dad Maheer ma na dayan gefen Ammar yana bayansu yana waya ta saka AZIZ maida hankalinsa akan wayar sbd sunan maganin dayaji ya ambata take ya fara zargin shine dr din amma kuma yana buqatan tabbatarwa dan haka a natse ya dago ya juya ya kalli Sayd wanda shima take ya fara searching sunan maganin dayaji ammar din ya ambata. Shigowansu ta saka gurin gaurayewa da kamshin turarukansu, Qamshin turarensa ne ya fita daban sbd shine baqo a cikin kamshin da suka saba dashi a gidan dan haka take kai tsaye su jannah din daya shiga hancinta ta dago ahankali tana kasa kallansa sbd Ammar daya futo daga bayansu yana kashe wayarsa idanuwansa akanta cikeda tsananin sonta yake kallanta yana bude baki ba sauti yace "Hey love" Kan Ammar din ta sauke idanuwan nata da suka kasa sauka akan LIMBA sbd kwarjinsa cika mata ido yake duk da tana jin tana buqatan qare masa kallo dan taga abinda yake hanata kallan fuskan nasa amma bazata iyaba. Ammar din take kallo haryazo gefenta y zauna. Falaq kuwa tashi tayi daga gefen falaq din tana zuwa gurin Daddynta tana cewa "Besty Muna gama dinner mu tafi gida yau inasa labari sosai da zan baka wanda Jan ta bani" Cikeda farin cikin gaske take maganar tana zaunawa gefensa. Fuskanta ya kalla cikin idanuwansa da kaunarta ce kadai basa iya biyewa ya bude baki a natse da sautinsa me dadi yace "Ok Falaq Aziz na shirya sauraranki har asuba" Dariyar jin dadi ta sake tana kallan jannah da kanta yake kan abincin dayake gabanta tace "Jan i told you he is the best" Dagowa jannah din tayi tana dan sake murmushi tareda daurewa ta saukar da idanuwanta akansa zuciyarta na rage bugawa da sauri tana bugawa a hankali da wani irin sanyi, Kasa dauke idanuwanta tayi akansa tanajin idanuwanta na neman tara hawaye takaicin kanta data kasa dauke kallanta akansa shi kuwa sam baisan da wata halittarta a gurinba bare ya kalli direction dintaba. Fiddausi ce tai serving nasa sbd itace ta saba hakan ta kuma san tsarin cin abincinsa dan haka tana gama serving nasa cikeda nutsuwa da kiyayewa falaq ta zubawa abincin kadan kafin mama ma tukuna ta juya tabar gurin. Abincin sukeso maganar falaq ce kadai take tashi a gurin magana daya biyu saita ambaci jannah wadda ita kuma gabaki daya take neman rasa kanta sbd tinani da bugun zuciyarta da suka hanata sukuni komai ta kasa ci. Ammar daya lura da yanayinta kallanta yayi yana ajiye spoo dinsa ahankali yana miqa hannunsa daya ya dora akan nata yana bude baki yace "Love,yaya dai? You okay??? Sai alokacin AZIZ ya dago idanuwansa ya saukar a inda take din kai tsaye akan hannun Ammar dayake kan nata sbd sunan saya kirata dashi a kunnensa ya sauka. Idanuwansa da bai dauke akan hannuwansu ba yana kalla cikin fahimtar abinda yake wakana kai tsaye a tsakaninsu ta dago idanuwanta ta kallesa suna taruwa da hawayen takaicin kanta da abinda yake shirin faruwa sa zuciyarta taga inda yake kalla Ahankali ta janye hannunta daga na Ammar din tana miqewa kai tsaye tabar gurin tana barin hawayenta gangarowa dan tabbas mutuwa zatai idan tabari wani abu ya shiga zuciyarta wanda bana Ammar dinta bane. Ammar miqewa yayi shima yana bin bayanta cikin mamaki me girma da damuwar ganin yanayinta idan ba wani abinne yake damunta. Kallo daya Yayiwa bayan Ammar din dayabi bayanta kaman zai fasa kuka sbd yanayinta ya dauke idanuwansa yana sake wani gajeran murmushin dabai fitoba yana tinanin kenan Ammar shine 'dan Zeynab Zad da akace ta rasu da ciwon zuciya itama tinda gashinan shine aure zai shiga tsakaninsa da jannah Zad wadda bazai taba barin su samu wannan farin cikinba. #MAMUH ZAFAFA BIYAR KALBIM 500 mamuhgee A DUNIYATA 500 Huguma AJIYA A DUHU 500 Billyn Abdul KIRJIN ME HANKALI 500 Miss xoxo Pay at 0022419171 AccessBank Maryam sani gummi Shedan biya 09033181070 Or mtn vtu at 09032345899*_Arewabooks@Mamuhgee_* 49 *ZUZEAM VENTURES* Best APHRODISIAC (kayan mata) 08144015291 Aslm barkanmu da wannan lokaci Ina Mai farin cikin sanar daku cewa Zuzeam ventures takawo maku ingantattun magunguna masu inganci cikin Aminci Muna da kaya kamar haka Mallaka Maganin sanyi Maganin cire tumbiMaganin farin jini Maganin matsiMaganin mata Maganin sa ni’ima da dandano Dulka Amare Set na gyran jiki Set na amarya Tabaje tsumin Gomba Xuma kiba ta hips and Brest Magungunan gyran Brest Magungunan Karin hips Maganin sliming Muna da kaya masu inganci cikin sauki da rahusa Ina wadda keneman mallaka sahihiya quaranty wlh hajiya kixo ga zuzeam ventures xakiji ddin mallaka duk fadin ran ogah duk fadansa wlh sai yyi sanyi 08144015291 Idan maganin mata kikeso akwai Idan gyran jiki kikeso gyran fata gyran Brest magungunan sa kiba da hips DOMIN samunta Kai tsaye kira wannan no 08144015291 DOMIN mgn da ita whatapp 08144015291muna tura kayanmu ko ina cikin iKon allah 🥰👌🏻 Bononza Bononza Tsimin mangoro 1k🥭 Tsimin dabino 1k Gumba ukku balai 700 Gumba aya da nonon rakumi 700 Garin kafi ciccibi 500 Garin bata gaban kishiya 500 Matsin mallaka tada zaune tsaye 2500 Turaren mallaka ba aba mai kishiya 2500 Total kayan 9500 Za a bakisu akan 4200 Kuma mutun goman farko nadakyautar Abun 2k 🗣️🗣️🗣️🗣️🗣️🗣️ ASSALAMU ALAIKUM ALHAMDULILLAH YAN UWA NEW PROMO YA KAMMALA💃🏽💃🏽💃🏽😁😁😁 da 6k dinki ki kwashi kayan 12k hajiyata 💃🏽💃🏽💃🏽😃🙃Kazar gadali ta mallara Rabi 3500 Tsimin gam gam 1500 Ruwan kara zunzurutun dadı😋800 Garin 7in1 1k Gumba 3 balai 500 Gumba kwakwa da dabino 500 Na Infection 1k Garin zunzurutun dadi 1200 Matsin ba a fira d wando 500 Matsin infection mai matse mace gam 500 12k All at 6k https://wa.link/l1gcz8 kedai dannan link dinnan don samun naki ki maza kiyi bucking koda kudinki saida Rabonki ************* Abu daya ya sani shine idan akai auren bazai samu damar juya rayuwar jannah din ba,. Baya buqatan komai akanta ita zuciyar datake bugawa a kirjinta kadai yake buqata dan hakanne bayajin wannan auren da Ammar yake jira zai tabbata sbd daga lokacin data zama matar wani ta shiga karkashin inuwar aure da kusan tabata tamkar keta hurumin ubangiji ne dan haka auren na buqatan dakatawa idan y gama da ita Ammar din zai aure gangar jikinta. Spoon ko daya baiyi da abincin ba kaman yanda falaq ma bataci komaiba surutu kawai take sbd ganin baici komaiba. Miqewa sukai suka fito zasu wuce bayan ya basu cikakkiyar daman samunsa a office ko gidan dan cike dukkanin takardun business da zasu kulla. Cikeda farin ciki suka fito rakasu harabar gidan bayan Dad yayiwa falaq kyautar dollars hakama Maheer kyautan maqudan kudi yayi mata duka babu wanda ta karba da hannunta Fiddausi ake bawa ta riqe mata. Mimi ma turaruka masu tsadar gaske tayiwa mama kyauta ta bawa Fiddausi kudi itama. Falaq har daki taje ta sanarwa jannah tana jiran kiranta da zuwanta. Gyada kai kawai jannah din ta samu damar yi tana kasa kallan falaq da fuskansa ma take gani a kan ta falaq din sbd kammaninsu. Motocinsu suka hau suka bar gidan mama na jin tsananin farin cikin kasancewa cikinsu da kuma kaunar Jannah dataji tanayi musamman sbd kaunar dataga ta kullu tsakaninta da falaq dan haka take tinanin Auren AZIZ da jannah ya shigeta dan da alama falaq ma zata amsheta tinda sunfar sabawa dan haka zata bari falaq din ta sake sakewa da shaquwa sa jannah din ta yanda zataji tana sonta a matsayin ta zamo matar daddynta hakanne kadai zai iya sakashi tinanin aurenta sbd babu abinda falaq tace tanaso da zaiyiba indai bai saba addiniba. Kudin da aka bawa falaq suna isa gida sayd ya bawa latif su gaba daya sbd ko cikin gidan baa buqatan su shiga. Sayd daya gama tattara bayanansa akan familyn tsaf na karantar da yayi musu din a wuni daya tsayawa yayi a gaban AZIZ din yafara masa bayani cikin nutsuwa da cewa "Tin muna can na saka an turo man sauran bayani da muke buqatan sani, Ammar Zad jannah ce kadai abinda zai rasa ya zare tareda bayyanar da kansa ta wani bangaren sbd an tabbatarda irin tsananin dayake mata ya wuce hankali hakama yanada trauma tin ta rasuwar mahaifiyarsa and zai iya yiyuwa shine likitan da muke nema a familyn sbd mahaifiyarsa da jannah ciwo dayane da su so zaifi zama sauki garesa kokuma burin karantar ciwon sbd maheer dai komai na familyn a hannunsa yake baida lokacin komawa sake karatun likita, Saleem kuwa a wancan lokacin bai isa zama likitan da har zai iya shiga tiyatar zuciyaba dan haka Ammar zad shine komai nasa yake nuni da zamansa likitan familyn...." Katsesa AZIZ yayi cikin gundura da jin saukan sunayensu a cikin lafiyayyun kunnuwansa masu tsarki da cewa "A farraqe nake buqatan ganinsu, Su fara samun second thoughts akan junansu, Su fara jin suna zargin junansu, Kowannensu ya fara son kansa ta yanda idan suka fara fuskantar matsaloli da masifar datake tafe kansu zasu rasa gurin tattaunawa da junansu dan neman mafita ko neman sauki, Idan basu farraqa ba samun nasara akansu zaiyi dauki lokaci, Bazan iya daukan lokaci ina tarayya dasuba sbd hakan na kona jinina da azababben baqin cikin ganinsu kadai dan haka ina buqatan rabewan kansu da bullowan matsala me girma a tsakaninsu dan hakanne zai saka sirrinsu fara fita coz a haka bazasu taba barin komai nasu ya fita ba komai kankartarsa sbd kuna kiyayewa.. Sayd shiru yayi yana shiga dogon nazari akan hakan dan kuwa neman abinda zai farrakasu zai dauki lokaci sbd duk dukiya da abinda zasu mallaka ko su rasa bazai taba rasa kansu sbd ba qaramin so sukewa juna ba familyn wanda shine abinda suka tabbatar a yau din, Dan haka idan suna neman abinda zai farraqasu to sai abinda suke tsananin so dukkaninsu ba kuma zai kasance dukiyaba, To menene??? Fitowa sayd yayi yana shiga tinanin me zurfi da neman mafitar dazai gabatarwa AZIZ din goben dan da alama LIMBAn baida lokaci batawa akan zaadens din sosai kawai rusasu yake son farawa akan lokaci to amma kuma dole suna buqatan cikakkiyar evidence akansu sbd so yake tin daga qasa ya rusasu har sama ta yanda babu kowane irin sauki bayan na mutuwa da zasu ringa nema sa kansu. Sayd na ficewa Falaq ta shigo sanye da kayan bacci riga da wando masu kauri sai hula akanta ta ipad dinta a hannu ta zauna gefensa tana shigewa jikinsa ta bude ipad din tana cewa "BestDaddy kalla hoton da mukai da jan, She's very beautiful am starting to like her tanada kirki yanzu ba kaman haduwanmu na farko ba" Idanuwansa ya sauke akan fuskan jannah din yayi mata kallo daya yana dauke idanuwansa wani dacin me karfi yana cike maqoshinsa zuwa kirjinsa. Labarinta falaq tafara basa yayi shiru idanuwansa akan bakin falaq din kunnuwansa basa akan abinda take fada sautin muryan Ummitah kawai yakeji acikin tata sbd kusan babu abinda ta baro na Ummitan, Tausayin falaq dinne yake yanka zuciyarsa yana ratsawa sbd tana magana kokarin fara kaunar wadda zuciyar mahaifiyarta ke bugawa kirjinta bayan an kashe tata mahaifiyar sbd wannan din ta rayu.... Rufe idanuwansa yayi Ahankali sbd jan da sukai radadin zuciyarsa na bayyana a cikinsu, Zaadens sun masa mummunan raunin da har abada duk abinda zai musu bazai warkeba sedai kuma zai tabbatarda dashi dasu ne zasu dawwama a cikin wannan radadin dashi kansa yake fatan inama tasa zuciyar aka cire yabar duniya ba Ummitahba, Zai tabbatarda ya gane waye asalin likitan da shine da hannunsa ya cire zuciyar Ummitah a cikin familyn dan kuwa idan Ammar ne to tabbas saiya rabasa da abinda yafiso a duniya fiyeda komai ya Tabbatarda ya gama zarewa trauma dinsa ta gama haukatar dashi, Zarewa yakeson yayi wanda zata sakasa illata kansa da kansa... Anan bacci yafara daukanta dan haka tadata yayi ya kama hannunta yakaita har dakinta bayan yayi mata adduoi ya rage mata ac sosai kafin ya rufeta ta kashe haske ya fito ya fice. Yana zuwa dakinsa wankan yayi shima ya fito sanyeda bathrobe ya tsaya gaban mirror yayi abinda zaiyi ya saka kayan bacci offwhite na ryaiss ya kwanta yana rufe idanuwansa dan dakatar da tinanin komai dake cikin kansa sbd lokacin baccinsa lokaci hutawansa ne. *******washe gari sai guraren 10 ya fito sanye cikin Armanis da wata shegiyar agogon dake daure a hannunsa. Fresh fuskansa sai fidda wani sirrin kwarjini take da haiba, Breakfast yayi tareda su kafin ya fito tareda sayd daya gama shirya komai. Yau zasu fara shiga office kuma yaune zasu tabbatarda hadewansu da Zaadens da kuma bayyanawa duniya dan haka koda isa securities ne tako ina sbd su kansu zaadens nada wani irin tsoro da securities dan haka kusan a tare suka iso kamfanin. Yan media ne a cike gurin suna isowa tako ina hotuna da tambayoyi ake jeho musu. Gurin a cike yake hakama ma'aikatan kamfanin me tsananin girm tin daga manya harna qasa suna harabar gurin dan tarbansu. Kai tsaye sukayo babu bata lokaci aka bi formalities aka saka hannu a komai wanda kai tsaye sunan JANNAH ZAD ne a rubuce ga kowace takarda me mahimmancin zaadens dan haka ya zubawa sunan ido kafin ya dago ya kallesu daya bayan daya suna cikin farin ciki da sakewa. Hannu ya saka akai sealing komai suka miqawa juna hannu yana cewa "Zamu bar tarihi" Cikin yadda da hakan Dad yace "For sure" Take aka dauki hotunansu ana yada labarai d jaridu da komai. Meeting suka shiga wanda sun jima kafin suka fito basu bar kamfanin ba sai yamma da haka kowa gida ya nufa cikin samun nutsuwan samun abinda duka sukeso.. Shiru yayi a hanyarsu ta zuwa gidan yana tinanin wane irin so ne sukewa 'yarsu sbd yasan ba irin wanda yakewa Ummitah bane dan bazai iya kashe ko dabba ba akanta sbd bayason hakkin hakan ya tabata ko yayane, Wane irin so ne yake sakawa ka kashe wani kisa me muni dan ka raya naka?? Sun san so me tsananin sbd sunawa tasu yar amma basusan meye qiyayya da tsans me tsananin gaske ba akan abinda kakeso dan haka zai nuna musu tareda banbancin a bayyane dan haka Indai Jannah ce abinda Ammar yafiso fiyeda nasa ran to zai tabbatarda bai mallaketa ba har abada, Zai tabbatarda bata zama tasa ba, Ba Ammar kadai ba kaf familyn zai fara rabasu da abinda sukeso ya juyar da rayuwarta zuwa abinda basu taba zataba,zuwa abinda zai ringa yanka zuciyarsu kowane seconds suna gani amma basada iko ko daya akanta, Zai gama kashe rayuwarta kafin ya barmusu gangar jikinda babu amfanin dazai musu bayan rufewa. Dago idanuwansa yayi ya kalli time din agogon hannunsa ya bude baki a natse yacewa sayd "Wane tsawon time mace take dauka ta fahimci she's in love? I want someone to fall madly In love" Da sauri sayd ya juyo ya kalli AZIZ din wanda fuskansa take a kame kaman ba shine yayi maganarba. Abinda tin jiyan yake yawo aran sayd dinne ya kasa fada yake tinanin zai tabbata dan kuwa farraqa tsakanin zaadens shine Jannah ta kamu da son wani so me karfin da zata fada da bakinta Hakan na faruwa bazasu taba hanata auren wanda takeso ba sbd bazasu taba mata dole ba hakama bazasuyi tinanin Ammar ba a wannan lokacin wanda hakan ne zai kawo babbar barakar da ake nema a hakan kuma yasan har abada AZIZ bazai taba auren wadda take dauke da jinin zadens ba ajikinta. #MAMUH ZAFAFA BIYAR KALBIM 500 mamuhgee A DUNIYATA 500 Huguma AJIYA A DUHU 500 Billyn Abdul KIRJIN ME HANKALI 500 Miss xoxo Pay at 0022419171 AccessBank Maryam sani gummi Shedan biya 09033181070 Or mtn vtu at 09032345899*_Arewabooks@Mamuhgee_* 50 *ZUZEAM VENTURES* Best APHRODISIAC (kayan mata) 08144015291 Aslm barkanmu da wannan lokaci Ina Mai farin cikin sanar daku cewa Zuzeam ventures takawo maku ingantattun magunguna masu inganci cikin Aminci Muna da kaya kamar haka Mallaka Maganin sanyi Maganin cire tumbiMaganin farin jini Maganin matsiMaganin mata Maganin sa ni’ima da dandano Dulka Amare Set na gyran jiki Set na amarya Tabaje tsumin Gomba Xuma kiba ta hips and Brest Magungunan gyran Brest Magungunan Karin hips Maganin sliming Muna da kaya masu inganci  cikin sauki da rahusa Ina wadda keneman mallaka sahihiya quaranty wlh hajiya kixo ga zuzeam ventures xakiji ddin mallaka duk fadin ran ogah duk fadansa wlh sai yyi sanyi 08144015291 Idan maganin mata kikeso akwai Idan gyran jiki kikeso gyran fata gyran Brest magungunan sa kiba da hips DOMIN samunta Kai tsaye kira wannan no 08144015291 DOMIN mgn da ita whatapp 08144015291muna tura kayanmu ko ina cikin iKon allah 🥰👌🏻 Bononza Bononza Tsimin mangoro 1k🥭 Tsimin dabino 1k Gumba ukku balai 700 Gumba aya da nonon rakumi 700 Garin kafi ciccibi 500 Garin bata gaban kishiya 500 Matsin mallaka tada zaune tsaye 2500 Turaren mallaka ba aba mai kishiya 2500 Total kayan 9500 Za a bakisu akan 4200 Kuma mutun goman farko nadakyautar Abun 2k 🗣️🗣️🗣️🗣️🗣️🗣️ ASSALAMU ALAIKUM ALHAMDULILLAH YAN UWA  NEW PROMO YA KAMMALA💃🏽💃🏽💃🏽😁😁😁 da 6k dinki ki kwashi kayan 12k hajiyata 💃🏽💃🏽💃🏽😃🙃Kazar gadali ta mallara Rabi 3500 Tsimin gam gam 1500 Ruwan kara zunzurutun dadı😋800 Garin 7in1 1k Gumba 3 balai 500 Gumba kwakwa da dabino 500 Na Infection  1k Garin zunzurutun dadi 1200 Matsin ba a fira d wando 500 Matsin infection mai matse mace gam 500 12k All at 6k https://wa.link/l1gcz8 kedai dannan link dinnan don samun naki ki maza kiyi bucking koda kudinki saida Rabonki ************* A zadeens sabuwar farin ciki da nutsuwar samun abinda sukeso sike ciki wanda ya saka walwalwansu ya dawo musamman sake fahimtar AZIZ LIMBA billionaire ne daidai su kuma kuma yakai yanada dukkanin wasu irin matakai dasuke tinani harma ya zarce wasu sbd power dayake da ita shima danma kwata kwata baya hulda da duk abinda ya shafi politics dan hakanne ya sake tsayuwa da kansa dan shi kadai babu saka hannu ko hanyar kowa a lamarinsa tsaye yake qam a AZIZ AY LIMBA  dinsa, Yanada wani irin kwarjini da izza tareda kamewan datake saka da yawa kasa tinkararsa, Bayada tsoro ko shakkar kowa da kowane irin matsayi sbd yanada karfi da ikon dayafi na manya da yawa sbd dukiyace me magana, Baida son hulda sosai da mutane sai wanda suka cancanta dan hakanne takowane bangare yayiwa Zaadens dari bisa dari dan haka sukejin su da shi alaqace ta riga ta kullu har abada sai mutuwa. Maheer cikin walwala da kwnaciyar hankali yake sauraron Anny datake jin duk majar da akai dashi da zaadens din bata ishetaa sbd komai zai iya zuwa karshe dan haka ita jini kawai takeson a hada dashi dan ta hakanne zasu zama shi ya zama su,dukiya kuma xasu mallaki duk wasu billions da suke buqata ko suka rasa a crisis din daya wuce dan haka zaunawa tayi kan kujera  gaban dresser tana kallan fuskanta a jikin mirror din ta miqa hannunta ta dauki cleanser ne tsada tana goge fuskanta ahankali tana kuka kallan mijinta dayake  sune bakin gado yana kashe wayarsa ya ajiye gefen bedside ta bude baki Ahankali tana dora kafa daya akan daya cinyoyinta na bayyana suna sheqi sbd rigar baccin jikinta short ce sosai me santsi ta bude baki tana kallansa ta cikin mirror tace "Baby kana ganin zamu iya zama tamkar family daya da LIMBA? Zamu hade gaba daya mu zama daya tamkar ahali kaman yanda muke so kuwa?? Dagowa yayi ya kalleta da murmushi akan fuskansa yace "Mun hade already ai baby meya rage tinda munxama business partners hakama familynmu sun hadu an kulla zumunci" Gama shafa turarukanta na bacci da goge gogen fuskanta tayi tana tasowa ta nufo lafiyayyan gadonsu ta zagayo inda yake ta zauna gefensa tana miqa hannunta akan kirjinsa tana shafawa zuwa wuyansa da kunnensa ya lumshe idanuwansa yana saukesu akanta tareda bata dukkanin nutsuwansa sbd Shafan kunnuwansa zuwa wuyansa datake dole hankalinsa kaf ya tattaru akanta. Tace "Partnership na business da wasu huldodin sunada lokacin qarewa da yankewa komai daren dadewa amma zamowa family har abada ne,koda an samu matsala to anriga an zama familyn, AZIZ LIMBA ba wanda zaadens zasu bari su rasa bane har abada, Yanada dukkanin abinda kuke buqatan wanda zaku hada komai dashi ya sakance, He's very very powerful, a billionaire,he has d biggest connections,he's talented,sharp,genius Almost perfect in komai da komai, i dont see any reason da zai saka kuyi wasa da kasa maidasa family, Haduwan arzikinsa da power dinsa da namu shine zai saka Zaadens su zama unbeatable,untouchable,more and more power zamu sake tsayuwar da babu abinda zai taba shaking namu sbd duk wanda ya sakomu gaba ko waye yanada saa babba sbd a strike daya yayiwa Zaadens girgizan daya tin kakanni baa taba samun wannan zubewan ba" Shiru maheer yayi yana shiga tinanin maganganunta da tabbas shi kansa jin yake AZIZ din bai shiga hannunsu yanda ya kamata ba sbd kaman yanda Dad yakeson LIMBA da baida mutane a Nigeria su zama sune wainda sukafi kowa kusanci dashi, Sunason su kasance sune kadai family na biyu dayake da, Suna son ya zamana komai nasa sunsamu kusancin da sukeda kusan access da komai na tarin businesses nasa. Anny fuskan Maheer din take kalla tana ganin yanda yake shiga tinani da nazarin maganarta tace "Yanxu da ace akwai wata princess din a familyn nan da Aure kawai zamu hada dashi ta yanda komai dadewa dai dukiyarsa kaf zata zama ta ita da yayanta ne kuma tinda zaadens zasu zana sirikansa Biyayyan da binku zaiyi sosai Amma babu damar hakan yanzu sbd babu wata 'yar sai Jannah wadda Ammar ne wanda zaa aura mata ita kuma ta kasa tantance ba son aure take masa ba na yayanta dayake tsananin sonta ne kawai take masa, Tausayima take bani sbd ta rasa gane me zuciyarta ke so kada azo ayi auren ma daga baya ta gane ba son aure take masa ba ta shiga damuwar da zai saka ciwonta dawowa" Dagowa Maheer yayi ya kalli Anny din cikeda mamakin maganarta data kasa zama abar dauka ta wani bangaren. Cikin mamakinsa dayake sake bayyana yace "Jannah na Ammar Soyayyan da sukewa  junansu a bayyane yake, Tayaya ma zakiyi tinanin Jannah ba son Ammar takeba, Tin tana yarinyarta da soyayyarsa ta taso ta girma,babu wani dan adamn dai da jannah zata iya so a duniyar nan so na aure idan ba Ammar ba, Shi kansa kina sane da idan yaji maganar nan ta bakinki zai iya zarewa so kibar maganar nan iya nan ta jannah ba aurensa takesoba kadama na sake jin kin fada" Kwantar da kirjinta tayi ahankali kan nasa tana zagaya hannuwanta ta rungumesa tana cewa "Bazan sake fada ba amma kuma ka saka ido sosai akan jannah din ka fahimci abinda nakeson ka fahimta da kanka idan ka karanci komai zabinka ne ka bari ayi auren ta shiga damuwa kokuma a bari ta samu wanda takeso" Shiru yayi mata sbd baima son jin maganar kawai dai kaman yanda ta fada a farko da ace akwai wata yar a familyn tabbas zasu basa aurenta dan kawai su zama familyn gaske ba wai iya business partners ba duk da hakan zai tattauna da Dad suji yanda zasu sake shigar dashi jikinsu sosai amma bazai iya fadawa dad din maganar da Anny ta fada ba akan Ammar da jannah. Washe gari breakfast familyn sukai gaba daya a dining, Idon Maheer akan jannah yake wadda ta zauna gefen Ammar tana kallansa sbd irin kallan dayake mata kaman zai bude zuciyarsa y sakata ciki ya rufe kowama y dena ganinta. Wani Murmushi me sanyi ta sakar masa wanda baya tattareda asalin farin cikin daya fito daga zuciyar datake cikeda tsananin so. Anny data lura da yanayin yanda Maheer yake kallan Jannah yana kasa hana zuciyarsa karantar yanayinta sbd Anny ta riga ta jefa masa tinani da wasi wasi. Murmushi Anny ta sake tana kallan Jannah tace "Jan yau ne zakije LIMBAs gurin daukan Falaq Aziz? Inaga zamu tafi tare inason fitan yau nima na yi hayaniya" Dagowa Jannah tayi ta kalli Anny din wadda taci gaba da cin abincinta kaman ba ita tai maganarba hankali kwance. Dad cikin kulawa da tsananin kauna yace "Jan,yau din zakije? Falaq bata sakaki hayaniya sosai kada kiyi stressing kanki fa kinsan condition naki duk da komai lafiya kalau ne amma dai karki biye mata yarinya ce ita kuma lafiyayya kada kije kiyita tsalle kina wahalanda kanki" Cikin sakewa ta dago tace "No dad,banajin sauyin yanayin komai, Zan kula sosai insha Allah" Ammar ne ya kalleta yana ajiye fork din hannunsa yace "Are you sure love" Gyada masa kai tai tana murmushi tace "Kaunar yarinyar nakeji sosai kaman nice na haifeta,inason kasancewa da ita sbd ina samun wani farin ciki mai sanyi dayake bani nitsuwa akan kuruciyata dana rasa" Tsit gaba daya gurin sukai suna zuba mata idanuwa sbd maganar daga zuciyarta take fitowa sbd yanayinta da idanuwanta suna nuna abinda yake zuciyarta ne ta furta ba wasa. Mimi cikin jin farin ciki tace "Falaq din nata shiga rai amma ban dauka sosai ta shiga zuciyanki hakaba" Dad da bai taba jin abinda jannah din ta bude baki kai tsaye ta furta tana kauna da tsananin nutsuwa hakaba kallanta ya sake yi yana karantar da gaske abinda ta fada tsananin kaunar yarinyar take dan haka take yaji shima yana kaunarta sbd duk abinda zai saka yarsa farin ciki da samun nutsuwa irin wannan yana sonsa da kaunarsa babu shakka ko tinanin komai. Maheer ma jin yayi wani sanyi ya sake shigar zuciyarsa sbd wannan ma wata hanyar sake samun kusanci da kauna ne me karfi tsakaninsu da LIMBA sbd shima a nasa bangaren duk wanda yake so da kaunar 'yarsa babu abinda bazai iya masaba dan haka zasu taya jannah kaunar 'yarsa sosai. Ammar shiru yayi yana kasa cewa komai tareda zubawa jannah idanuwansa tana sake murmushin da wannan karan tin daga zuciyarta yake fitowa sbd ta bayyana kaunar datakewa Falaq kuma familyn sun nuna farin cikinsu da hakan dan haka take murmushint me kyau tana cigaba da cin abincinta hankali kwance. Ammar jin yayi kaman cikinsa ya toshe haka kawai dan haka ya dauki cup din warm drink ya kai bakinsa yasha ahankali tareda ajiyewa ya dauki tissue ya goge bakinsa yana cewa ya gama. Kallansa Jannah tayi tana son nasa magana sai kuma ta fasa tana masa magana da ido dole ya fasa tashi ya zauna yana kallanta tana qarasa cin abincinta cikin jin dadi da kwanciyar hankali harma da farin ciki dan haka kawai taji tama matsu taje gidansu Falaq din. Suna gama breakfast din ta wuce bedroom dinta ta zauna tana dan wayoyi da dube dube a wayar tana kaida kawo har abincin dataji yana dan zaunu a cikinta kafin ta zare komai ta fada toilet wanka. Wanka tayi ta fito daure da towel blue ta zauna tana goge jikinta ahankali kafin tafara shafa tana duk abubuwan data saba na shiryawa. Doguwar riga ta saka maroon sai guraren 2 ta fito riqe da handbag ta Louis Vuitton sai wedges shoes na versace, Qamshinta ne yake tashi ahankali mai sanyi da dadi, Key din motarta ne a hannunta da wayarta datake texting falaq din saying she is on her way. Anny data shirya itama fitowan tayi sanye da boubou din wata tsadaddiyar black lace mara nauyi da hayaniya ko kadan da handbag din chanel sai heels da ita ta saba su take sakawa suka fito suna ficewa gidan. #MAMUH ZAFAFA BIYAR KALBIM 500 mamuhgee A DUNIYATA 500 Huguma AJIYA A DUHU 500 Billyn Abdul KIRJIN ME HANKALI 500 Miss xoxo Pay at 0022419171 AccessBank Maryam sani gummi Shedan biya 09033181070 Or mtn vtu at 09032345899*_KALBIM_* _Mamuhgee_ 51 *ZUZEAM VENTURES* Best APHRODISIAC (kayan mata) 08144015291 Aslm barkanmu da wannan lokaci Ina Mai farin cikin sanar daku cewa Zuzeam ventures takawo maku ingantattun magunguna masu inganci cikin Aminci Muna da kaya kamar haka Mallaka Maganin sanyi Maganin cire tumbiMaganin farin jini Maganin matsiMaganin mata Maganin sa ni’ima da dandano Dulka Amare Set na gyran jiki Set na amarya Tabaje tsumin Gomba Xuma kiba ta hips and Brest Magungunan gyran Brest Magungunan Karin hips Maganin sliming Muna da kaya masu inganci cikin sauki da rahusa Ina wadda keneman mallaka sahihiya quaranty wlh hajiya kixo ga zuzeam ventures xakiji ddin mallaka duk fadin ran ogah duk fadansa wlh sai yyi sanyi 08144015291 Idan maganin mata kikeso akwai Idan gyran jiki kikeso gyran fata gyran Brest magungunan sa kiba da hips DOMIN samunta Kai tsaye kira wannan no 08144015291 DOMIN mgn da ita whatapp 08144015291muna tura kayanmu ko ina cikin iKon allah 🥰👌🏻 Bononza Bononza Tsimin mangoro 1k🥭 Tsimin dabino 1k Gumba ukku balai 700 Gumba aya da nonon rakumi 700 Garin kafi ciccibi 500 Garin bata gaban kishiya 500 Matsin mallaka tada zaune tsaye 2500 Turaren mallaka ba aba mai kishiya 2500 Total kayan 9500 Za a bakisu akan 4200 Kuma mutun goman farko nadakyautar Abun 2k 🗣️🗣️🗣️🗣️🗣️🗣️ ASSALAMU ALAIKUM ALHAMDULILLAH YAN UWA NEW PROMO YA KAMMALA💃🏽💃🏽💃🏽😁😁😁 da 6k dinki ki kwashi kayan 12k hajiyata 💃🏽💃🏽💃🏽😃🙃Kazar gadali ta mallara Rabi 3500 Tsimin gam gam 1500 Ruwan kara zunzurutun dadı😋800 Garin 7in1 1k Gumba 3 balai 500 Gumba kwakwa da dabino 500 Na Infection 1k Garin zunzurutun dadi 1200 Matsin ba a fira d wando 500 Matsin infection mai matse mace gam 500 12k All at 6k https://wa.link/l1gcz8 kedai dannan link dinnan don samun naki ki maza kiyi bucking koda kudinki saida Rabonki ************ Jannah ce take jan motar a nitse zuwa gidan wanda suna sake kusantar isa gidan bugun zuciyarta sauyawa yakeyi ahankali sbd hakanan batason ta hadu da Daddyn Falaq din dan haka koda Anny ke mata maganar Aurenta da Ammar daya kamata a bari sai komai ya sake daidaita batama jinta sosai sbd hankalinta da tinaninta nakan tinanin wanda a ko yaushe yake guri take samun kanta da jin zuciyarta na sauya bugu. Suna isowa gidan Securities dayake sun san da zuwan na Ms Jannah Zad wadda Falaq ta sanar musu dan haka babu bata lokaci aka bude musu suka shigo cikin tsananin girmamawa. Parking tayi gabanta na dan faduwa sbd ganin motocin datake da tabbacin yana gidan dan haka ta kasa fitowa motan saida ta daidaita bugun zuciyarta ta bude ta fito. Anny dake kallan mahaukatan motocin dake harabar gidan da tsarin gidan jin tayi komai ya burgeta sbd Allah bai bata godiyansaba dan a nasu gidan babu kalar jin dadi da duniyar da aka rasa a zadeens hakama gidan LIMBAs din ba fin nasu yayi ba kusan gogawa akeyi kawai dai dan nasa tsarin yana sabo ne kuma daban da nasu amma suma nasu gidan kaman Aljannar duniyarne to amma ganin takeyi duk kaman nan din yafi sbd tsatsar zuciya. Falaq datake jiran zuwan jannah din tin safe ta hana kowa zama anata shirin zuwan jannah Me aikin data saka tsaron harabar gidan dan ta sanar mata idan sun iso tana ganin shogowan motarsu juya da sauri taje ta sanarw Fiddausi sbd ita kadai keda ikon zuwa hanyar bangarensa a cikin masu aikin gidan kuma gashi falaq din na gefensa ta hanasa fita tace se baquwanta tazo sbd a rayuwarta wannan shine karo na farko da zatai baquwan kanta shiyasa takejin kaman zata taka jariri sbd murna ta hana kowa sukuni. Fiddausi data iso kofar palonsa karamar doorspeaker dake gurin mara qara ta taba tareda kai bakinta cikin nutsuwa tace "Baquwan Falaq Aziz ta iso" Daga ciki akwai qaramar speaker da ake jin zancen wanda yayi daga wajen kofar ba tareda hayaniyaba dan haka Falaq dake gefen Daddynta tana nuna masa dukkanin firanta da Jan a ipad dinta tana jin hakan miqewa tayi daga jikinsa tana murmushi me tsananin kyau tace "BestDaddy special guest dina tazo" Miqewa tana nufar kofa ta fice da sauri tana barin ipad dinta a jikinsa. Kallan ipad din yayi hotonta ne dana jannah din dayake cikin chats nasu yake bayyane. Hannunsa ya saka ya danna lock ta rufe kafin hoton lockscreen dinta ya bayyana wanda yake hotonsa ne shida ita tana jikinsa tana dariya sosai cikeda tsananin kaunarsa da bata hada da komaiba. Harabar gidan ta nufa da gudu Fiddausi na biye da ita cikeda farin ciki tayi kan jannah din ta rungumeta tana dariya. Itama jannah din dariyar takeyi tana kama hannunta sbd jin numfashinta na sauyawa sbd gudun datai ta janyota gabanta tana cewa "Ki dena irin wannan gudun okay." Gyada kai jannah din ke yi tana dan hadiye yawu sbd numfashinta dayake fita da karfi tana jin kaman kirjinta bazai dauka. Ciki suka nufo Fiddausi na musu sannu da zuwa tana wucewa kitchen da sauri ta daukowa Falaq din da numfashinta yake sauyawa sosai ruwa. Mama data fito su gaisa ganin yanayin falaq din cewa tayi "Yaya dai take wannan numfashin? Fiddausi data bude mata robar ruwa tana zubawa a glass cup miqa mata tai bakinta tana cewa "Gudu tai sosai" Jannah ce ta karba cup din tana cewa "Sha ruwan and calm your self tukuna kinji" Bude baki tayi tasha ruwa kadan tana kokarin cewa she's ok amma ta kasa ta riqe hannun jannah tana kallanta. Anny ce ta gaida mama suka gaisa cikin sakewa tana musu barka da zuwa. Jannah ma gaisawa sukai da maman mama na tambayarsi Mimi cikin sakewa da farin ciki sosai da zuwansu. Fiddauci ganin yanayin Falaq din ya sakata kasa sakewa tace "Falaq muje dakinki ki dan kwanta ko some minutes ki nutsu ki samu ki dawo daidai kinji" Girgiza kai tayi tana rufe idanuwanta har lokacin hannunta na cikin na Jannah wadda take shiga damuwa ganin Falaq din kaman ba lafiya ba. Miqewa sukai bayan mama ta yadda da hakan itama tana riqe da hannun jannah suka isa bedroom dinta suka shiga jannah dince ta taimaka mata t kwanta ahankali zuciyarta na sake tsananta bugawa. Shafa fuskanta zuwa kanta jannah keyi cikin nutsuwa ahankali tana kokarin tayata daidaita numfashinta. Lumshe idanuwanta da suka dan sauya falaq tayi tana samun sassauci da daidaituwan bugun zuciyar ahankali. Mama da Fiddausi dake tsaye juyaw sukai sun ficewa mama na jin kwanciyar hankalin ganin yanda Jannah takewa falaq din tamkar uwa, Hakama falaq dinta na riqe da hannun jannah daya har lokacin. Mama ce ta nufi palon AZIZ din da kanta ta samesa yana waya a natse, Ganin yana waya sai bata ce komaiba ta juya zata fice yai sallama da wayar ya kashe yana cewa "Mama akwai wani abu ne?? Juyowa tai ta kallesa batareda ta dawo ba tace "Babu komai kawai naso magana dakai ne akan lokacin da yayi na aurenka ko dan samawar 'yarka cikakkiyar kulawa sbd bazaka so ace ta taso ba uwana ta qare a karkashin kulawan masu aiki da nannys batareda ta samu kulawa daga uwa ba har girmanta, Ga yanayi na ciwonta sai gaba yakeyi sbd yanzu daga gudu kawai tana neman rasa bugun zuciyarta.. Ajiye wayar hannunsa yayi yana miqewa ya nufo kofar yana cewa "Tayi gudu? Meyasa tayi gudun? Ina taje ne?? Mama bata samu amsasa duka ba tayi gaba tana cewa "Sbd murnan Zuwan jannah ta fita da gudun tarbanta.... Ko qarasa ji baiyiba ya fito yana nufar bedroom din jannah din wanda Fiddausi data kawo zata koma dakin kai wasu ruwan da drinks tana ganinsa tayi saurin dakatawa tana sauke kai qasa harya wuce ya nufi dakin ya bude kai tsaye ya shige. Budewa idanuwa falaq tayi tana ganinsa ta daga hannunta daya ta miqa masa tana narke fuska. Qarasowa yayi yana zaunawa bakin gadon tareda dagota gabaki dayanta kafin yayi magana ta kwanta jikinsa tana riqe hannunsa daya sosai. Cikin wani irin sauti dayake son nuna bacin ransa amma kuma bayason dagawa yarsa harshe dan haka tsananin kulawansa yana danne bacin ran yace "Meyasa kikai gudu? Akwai abinda yakai lafiyanki mahimmanci ne da zaki komai kiyi gudu, Meyene yakeda mahimmancin dazai sakaki irin wannan guje gujen? Don't you try that again kinaji na?? Gyada kanta tayi ahankali tareda dagowa tana kallansa zuwa lokacin bugun kirjinta ya dawo mata daidai sbd yanda jannah ta kula da ita. Bude bakinta tayi cikin kaunarsa tace "Ina murnan zuwan Jan ne, Amma bazan sake ba BestDaddy" Sai a lokacin datai maganar ma ya lura sa akwai wani a kusada su din dan haka ya juya idanuwansa akan jannah din wadda tinda ya shigo gurin kamo falaq da hannunt dayake cikin n falaq ya hada ya kamo zuwa jikinsa tai mutuwan zaune a gurin komai na jikinta na dena aiki sai zuciyarta dake harbawa kaman t falaq din. Kallo daya tai masa ta kasa sake dago idanuwanta ta sake kallansa qamshinsa kuwa dayake shigarta direct ba nisa komai na cikin kanta dena aiki yayi zuciyarta ce kadai take aiki wanda babu komai a cikinta bayan asalin zazzafar soyayyar dake neman fasa kirjinta wadda batasan ta ina,daga ina,ta yaya take shigartaba tana bin jininta.... Hawayen tashin hankali da tsoron abinda take ji a tsakiya da koina na zuciyar ne suka ciko mata idanuwa sbd jin take kaman ta fasa kuka ta bude zuciyarta ta fidda son me tsananin gaske take ji. Kallan asalin tsana da rashin kaunar duk jinin dayake yawo a duniya yake mata yana jin zafi na cike kirjinsa me karfin gaske zaiyi magana sai kuma ya fasa sbd maganan da ita is like wasting his energy and disrespectin his time a banza dan haka ya miqe yana juyawa yana cewa "Useless people everywhere" Ficewa yayi daga dakin yabar Jannah din na bin kofar daya fice da idanuwanta da sukai tsananin sanyi sbd a kunnenta kalmansa ta sauka duk da ba sauti sosai amma kuma ba kalman ce ta kashe jikintaba irin tsananin tsana da qin data hango cikeda fararen idanuwansa da suke qara kashe zuciyarta tako ina da azababbiyar soyayyar datake jin kaman kirjinta bazai iya riqewaba. Falaq cikin kulawa ta kama hannun jannah tana cewa "Na dawo daidai ki dena damuwa kaman Bestyn falaq koyaushe yana damuwa abu kadan idan ya sameni" Sunkuyar da kai jannah tayi tana sauke boyayyar numfashi me tsananin sanyi tana kunya da takaicin kanta. Fiddausi ce ta shigo da babban trey tana farin cikin dawowan falaq din daidai tana cewa "Duk murnan zuwan Ms jannah yana neman komawa ciki kina neman daga mana hankali da rana tsaka" Dariya tayi tana fita da sauri taje palonsa ta dauko ipad dinta tadawo tana zaunawa gefen jannah data dan sake tana magana da Fiddausi dake bata labarin kuruciyan Falaq din tana jin kaunar falaq din na sake ratsata. #MAMUH ZAFAFA BIYAR KALBIM 500 mamuhgee A DUNIYATA 500 Huguma AJIYA A DUHU 500 Billyn Abdul KIRJIN ME HANKALI 500 Miss xoxo Pay at 0022419171 AccessBank Maryam sani gummi Shedan biya 09033181070 Or mtn vtu at 09032345899*_KALBIM_* _Mamuhgee_ 52 *ZUZEAM VENTURES* Best APHRODISIAC (kayan mata) 08144015291 Aslm barkanmu da wannan lokaci Ina Mai farin cikin sanar daku cewa Zuzeam ventures takawo maku ingantattun magunguna masu inganci cikin Aminci Muna da kaya kamar haka Mallaka Maganin sanyi Maganin cire tumbiMaganin farin jini Maganin matsiMaganin mata Maganin sa ni’ima da dandano Dulka Amare Set na gyran jiki Set na amarya Tabaje tsumin Gomba Xuma kiba ta hips and Brest Magungunan gyran Brest Magungunan Karin hips Maganin sliming Muna da kaya masu inganci cikin sauki da rahusa Ina wadda keneman mallaka sahihiya quaranty wlh hajiya kixo ga zuzeam ventures xakiji ddin mallaka duk fadin ran ogah duk fadansa wlh sai yyi sanyi 08144015291 Idan maganin mata kikeso akwai Idan gyran jiki kikeso gyran fata gyran Brest magungunan sa kiba da hips DOMIN samunta Kai tsaye kira wannan no 08144015291 DOMIN mgn da ita whatapp 08144015291muna tura kayanmu ko ina cikin iKon allah 🥰👌🏻 Bononza Bononza Tsimin mangoro 1k🥭 Tsimin dabino 1k Gumba ukku balai 700 Gumba aya da nonon rakumi 700 Garin kafi ciccibi 500 Garin bata gaban kishiya 500 Matsin mallaka tada zaune tsaye 2500 Turaren mallaka ba aba mai kishiya 2500 Total kayan 9500 Za a bakisu akan 4200 Kuma mutun goman farko nadakyautar Abun 2k 🗣️🗣️🗣️🗣️🗣️🗣️ ASSALAMU ALAIKUM ALHAMDULILLAH YAN UWA NEW PROMO YA KAMMALA💃🏽💃🏽💃🏽😁😁😁 da 6k dinki ki kwashi kayan 12k hajiyata 💃🏽💃🏽💃🏽😃🙃Kazar gadali ta mallara Rabi 3500 Tsimin gam gam 1500 Ruwan kara zunzurutun dadı😋800 Garin 7in1 1k Gumba 3 balai 500 Gumba kwakwa da dabino 500 Na Infection 1k Garin zunzurutun dadi 1200 Matsin ba a fira d wando 500 Matsin infection mai matse mace gam 500 12k All at 6k https://wa.link/l1gcz8 kedai dannan link dinnan don samun naki ki maza kiyi bucking koda kudinki saida Rabonki ************* Jannah sakewa tayi sosai a dakin falaq din tana nuna mata abubuwa da yawa wanda komai na duniyarta akwai daddynta acikinsa, Maganarta da komai nata akan Daddynta ne hakama gabaki daya ta gama illata zuciyar Jannah din da idanuwanta da hotinansa dake yawo koina a cikin ipad dinta da dakin da har lokacin tana jin qamshinsa a hancinta yana qarasa illata zuciyanta. Abu dayane ta tabbatar a wuninsu gidan shine sonsa take da dukkanin zuciya da gangar jikinta batareda ta saniba a ganin farko datai masa tin baa nan qasar ba sedai kuma batajin ko sonsa zai kasheta zata iya barin kowa ya sani sbd Ammar zai iya rasa kansa akan hakan, Ita kanta ta zabi illan da dik sonsa zai mata data bari sonsa yafi karfin son datakewa Ammar. Anny a can dake fira da mama dukkanin yanda zata cusawa kauna da shaawar aurawa AZIZ jannah tayi a cikin dubara da salan zance sbd lura da maman na kaunar jannah a matsayin matar gidan. Tare sukaci abincin rana a dining banda mai gidan sbd babu wanda ya sake ganinsa kamanba ya fita baya gidan. Sosai suka sake Falaq taji dadin zuwansu sosai duk da basu fita ba sbd Daddynta ya hana sbd jikinta dayaso tashi dan haka a gidan suka shaqatansu jannah ta saki jiki da ita suka sake kulla kauna me tsafta da karfi. Sai yamma suka fito zasu tafi falaq na maqale gefen jannah din tana cewa tazo gobe da Allah su tafi inda zasu tafin. Gate aka bude motarsa ta sako kai a harabar gidan, Janye kallanta daga gurin jannah tayi tana cewa Falaq insha Allah idan har Daddynta zai bari goben zataxo ta dauketa su fita. Janta falaq tayi da karfi zuwa gurinsa daidai latif na bude masa motar yana fitowa. Kadan ya rage su fada masa ya tare Falaq da hannuwansa biyu yana kallanta fuskansa na sauyawa a natse yace "Ba na fada ki dena wannan gudun ba? Kan jannah ya maida kallansa a natse yace "Are you crazy or wat? Yarinya qarama kike sakawa wannan gudun? Dagowa tayi ta kallesa da idanuwanta dake sauyawa cikin mutuwar jiki da tsananin nauyin kirji sbd tinda take a duniya ko kallan banza batajin ta taba samun wanda ya mata ta sani bare ambatar mata kalma mara dadi bare me munin kiranta crazy dan haka taji kalman har zuciyarta amma bata iya cewa komaiba ta juya zata bar gurin Falaq tayi saurin riqeta tana dawo da ita tace "Daddy nice na jawota fa,inason ka bari gobe muyi fitan tinda yau ka hana pls pls Daddy" Bai kalletaba yana wucewa gaba yace "No" Binsa falaq din tayi da sauri tana rokonsa. Jannah kuwa ajiyar zuciya ta sauke tana juyawa ta nufi motarta. Anny kuwa Sayd ne daya gama shirinsa akanta yana fitowa mota daman ita ya nufa kai tsaye ya miqa mata envelope dake daukesa dollars masu yawa yace gashinan from LIMBA su qara mai a mota. Karba tayi tareda cewa thank you batareda ta nuna damuwa da kudinba. Mota ta bude tana shiga ta bude kudin ta duba batasan lokacinda ta furta "Hell yeah the great LIMBA" A lokacin ne jannah ta iso motar ta shigo ta tada tareda tadawa taja suka bar gidan ranta a bace. Suna isa gida kai tsaye dakinta ta wuce tan wurgi d handbag dinta akan gadon. Anny kuwa kudin da aka basu ta fadawa Maheer. Se dare ta fito cin abinci sanye da riga da wando masu dan kauri da hula suna gama cim abinci ta koma dakinta. Washe gari tinda safe falaq ta kirata t sanar da ita daddynta yabari su fita amma tareda Latif zasu ba itace zata tuqasu ba. Taso tace batada time amma jin farin cikin falaq din sai bata fada ba. Da rana Falaq din ta iso gidan tareda Fiddausi Latif ya kawosu suka dauketa suka fice. Basu dawoba sai dare, Duk da ta gaji saida ta ringa basa labari kafin taje tayi shirin bacci ta kwanta sbd sunyi sallolinsu acan. Washe gari ma sake fita sukai sbd falaq tace tanason kayan da jannah ta saka a fitansu na jiyan waton native wear dan haka kaya sosai Jannah ta siya mata suka bayar dinki wasu kuma ready to wear ne na daidai ita masu tsada sosai. **********Shaquwa a tsakanin Jannah da falaq yawa yafara sosai a cikin qanqanin lokaci, Duk yanda zai hana falaq ya saka mata qin Jannah din yayi amma kwata kwata hakan shine abu na farko daya kasa cire mata a ranta, Sosai take tsananin kaunar jannah, Sun zama kaman saanin juna sbd jannah sosai take biyewa falaq din wanda hakanne yake saka falaq jinta sosai aranta, A bangaren jannah kaunar datakewa falaq ta sirku ne da tsananin son dayake zuciyarta nasa, Fuskansa take gani koyaushe akan ta falaq, Murmushisu daya, Hancinsu da lips dinsu daya wanda so da dama zata kira Falaq video call ta zauna ta zuba mata idanuwanta tana kallan hancinta da lips dinta da kammaninta gaba daya da suke irin nasa. An saka falaq din school dan haka sun rage haduwa a maimakon dan lokacin da kusan kullum suna tare ko anan gidan idan tazo kokuma idan falaq da Fiddausi drivern falaq din ya kawosu. A bangaren mama ta bude masa wuta aure takeson ya fidda mata yayi kokuma ta nema masa matar da kanta wadda ba kowace take hari ba bayan jannah din. A zaadens kuwa Anny da Sayd ya gama kuncewa kai da barin kudi tini ta gama sauyawa Maheer tinani kwata kwata akan auren Jannah da Ammar sbd Tabbas ya yadda Jannah ba son aure takewa Ammar ba to amma ya kasa yadda da Cewan Da Anny tai Jannah da LIMBA suna son juna amma dai dole wannan karan yafadawa Dad sbd anfara maganar fara hidiman bikin Ammar da jannah din. Duk abinda zai hada jannah da LIMBA ta janye sbd ganinsa rikita tinani da nutsuwarta yake gaba daya gashi sun samu shaquwar familyn guda biyu sbd kusan yanzu sun zama tamkar family dan shaquwan tayi yawa. Ammar gabaki daya ya fara sauyawa sbd yawan ziyartar therapist dinsa yayi yawa sbd jannah dayake jin kaman zai iya rasawa dan haka ya bude wuta kawai auren yakeson ayi. Mimi ma auren take jira dan haka ana fara kokarin shirye shirye ta shiga farin ciki da murna. Jannah kuwa tinda aka saka lokacin auren wata daya me zuwa rasa sukunin zuciyarta tayi wanda duk yanda take boyewa tana kokarin nuna tsananin soyayyarta da auren love of her life jikinta ya kasa nuna hakan sbd sanyin datake yi hakama Anny tagama illata duk wani kuzari da karfin zuciyarta da zancensa da nuna mata irin soyayyar da zuciyarta ke masa ta hanata sukuni da zancensa duk yanda ta hada karfin hali ta danne abinda takeji akansa Sai Anny ta wargaza mata dan haka gabaki daya t sake zama abar tausayi. Maheer ganin lokaci na zuwa sosai ga jannah din tana wani irin rama kasa boyewa yayi ya tinkari dad da maganar jannah batason auren Ammar soyayyar dan uwace take masa irin wadda take musu su da suke uwa daya. Dad jin zancen yayi wani iri kuma ya kasa yadda da hakan dan haka ya kira jannah din sbd wannan zancen kunnowan tashin hankali da masifa ne sbd Ammar zai iya mutuwa idan ya rasa jannah hakama suma idan da gaske ne bazasu iya mata auren da batasoba dan haka akwai tashin hankali me girma a wannan lamarin. A bangaren LIMBAs kuwa falaq ta shiga damuwa sosai sbd Falaq bata farin ciki da auren da zatai dan haka ta koma musu kaman mara lafiya itama ta shida damuwa karshe gurin daddynta ta nufa a lokacinda ake maganar saura sati biyu bikin. Da Anny ta gama waya ta zauna ta kasa motsi sbd abinda Anny ta fada mata akan Jannah daddynta takeso akansa ne batason wanda zata aura batason ta bata mata rai ne tinda batason daddynta tayi aure taqi barin kowa ya sani. Shiru falaq din tayi cikeda mamakin kanta da bataji haushin hakanba amma kuma tanajin kaman bazata iya barin daddynta aureba amma kuma yayi mata alkawarin auren duk wadda ta kwanta mata a matsayin uwa indai batada illar da addini y sharadanta. Tan tsananin kaunar jannah da bazat iya barin tayi auren wanda bataso ba dan haka koma yaya take kishin daddynta zata bari Jan dinta ta zama matarsa kuma ita kadai ta yadda ta haifa mata kanne. Take taji ta gama samun nutsuwa da hakan sbd kaunar datakewa jan din duk ta gama rufe mata ido daman batason Ammar din nan ko kadan haka kawai. Kallanta yayi a lokacinda tazo ta zauna gefensa suna kan dining dukkaninsu gidan cin dinner. Fara cin abinci akai ta ajiye spoon dinta ta dago ta kalli Uncle sayd daya kalleta yana shirin tambayan lafiyanta ta ajiye spoon din hannunta idanuwanta na cikowa da hawaye tace "Daddy ka hana auren da zaayiwa Jan bataso Ina son ka aureta ita kadai karka kara auren kowa bayan ita kadai, Ita kadai nakeso as mum and ita kadai nakeson ta zama maman kanne...... Sarkewa Say yayi da white rice da egg sauce din dayake ci yafara tari da karfi. Mama ma sauran kadan din ta sarke Fiddausi data rude itama tana kawowa Falaq din yankakken pineapple ajiyewa tayi da sauri tana bawa mama ruwa hannuwanta na rawa kowa ya kasa dagowa ya kalli reaction dinsa gurin yayi tsit. #MAMUH ZAFAFA BIYAR KALBIM 500 mamuhgee A DUNIYATA 500 Huguma AJIYA A DUHU 500 Billyn Abdul KIRJIN ME HANKALI 500 Miss xoxo Pay at 0022419171 AccessBank Maryam sani gummi Shedan biya 09033181070 Or mtn vtu at 09032345899*_KALBIM_* _Mamuhgee_ 53 *ZUZEAM VENTURES* Best APHRODISIAC (kayan mata) 08144015291 Aslm barkanmu da wannan lokaci Ina Mai farin cikin sanar daku cewa Zuzeam ventures takawo maku ingantattun magunguna masu inganci cikin Aminci Muna da kaya kamar haka Mallaka Maganin sanyi Maganin cire tumbiMaganin farin jini Maganin matsiMaganin mata Maganin sa ni’ima da dandano Dulka Amare Set na gyran jiki Set na amarya Tabaje tsumin Gomba Xuma kiba ta hips and Brest Magungunan gyran Brest Magungunan Karin hips Maganin sliming Muna da kaya masu inganci cikin sauki da rahusa Ina wadda keneman mallaka sahihiya quaranty wlh hajiya kixo ga zuzeam ventures xakiji ddin mallaka duk fadin ran ogah duk fadansa wlh sai yyi sanyi 08144015291 Idan maganin mata kikeso akwai Idan gyran jiki kikeso gyran fata gyran Brest magungunan sa kiba da hips DOMIN samunta Kai tsaye kira wannan no 08144015291 DOMIN mgn da ita whatapp 08144015291muna tura kayanmu ko ina cikin iKon allah 🥰👌🏻 Bononza Bononza Tsimin mangoro 1k🥭 Tsimin dabino 1k Gumba ukku balai 700 Gumba aya da nonon rakumi 700 Garin kafi ciccibi 500 Garin bata gaban kishiya 500 Matsin mallaka tada zaune tsaye 2500 Turaren mallaka ba aba mai kishiya 2500 Total kayan 9500 Za a bakisu akan 4200 Kuma mutun goman farko nadakyautar Abun 2k 🗣️🗣️🗣️🗣️🗣️🗣️ ASSALAMU ALAIKUM ALHAMDULILLAH YAN UWA NEW PROMO YA KAMMALA💃🏽💃🏽💃🏽😁😁😁 da 6k dinki ki kwashi kayan 12k hajiyata 💃🏽💃🏽💃🏽😃🙃Kazar gadali ta mallara Rabi 3500 Tsimin gam gam 1500 Ruwan kara zunzurutun dadı😋800 Garin 7in1 1k Gumba 3 balai 500 Gumba kwakwa da dabino 500 Na Infection 1k Garin zunzurutun dadi 1200 Matsin ba a fira d wando 500 Matsin infection mai matse mace gam 500 12k All at 6k https://wa.link/l1gcz8 kedai dannan link dinnan don samun naki ki maza kiyi bucking koda kudinki saida Rabonki ************ Zubawa Daddyn nata idanuwanta duka falaq tai tana kallansa cikeda nutsuwa da tsananin son amincewansa duk da tasan bazai taba iya qin mata duk abinda ta furta tana so ba. Cikeda wani 'daci me tsananin gaske ya hadiye abincin dayake bakinsa batareda ya kalli kowa dayake gurinba sbd yanayin bacin rai mai tsananin daya shiga amma ya hanasa bayyanuwa dan haka baice komaiba kamarma baiji abinda ta furta dinba. Mama ce ta fara dagowa ta kallesa tana karantar yanayinsa sedai batace komaiba sbd tasan sarai yaji sedai zancen garesa kaman abune da bazai yiyu ba sbd ba auren yakeso ba baya gabansa. Sayd ma dagowa yayi a hankali ya kallesa yana karantar yanayinsa dayafi kowa iya sanin kowane yanayinsa meyake nufi, Zallan asalin bacin rai da zafi me tsanani ne yake hangowa a yanayinsa wanda ayau da ba Falaq ce ta furta zancenba tabbas da zaaga fushi da bacin ransa amma kwata kwata ya nade komai yabarwa zuciyarsa. Hawayen da Falaq din ke riqewa tinda Anny ta fada mata Jan son daddynta takeyi ta sake sbd ta wani bangaren da gaske kishin daddynta ya kawo wata a rayuwarsu take sosai hakama har ranta kishin Daddynta ya haifi wasu yayan dazai raba musu tsananin kaunar dayake mata take amma kuma ta wani bangaren yanda takejin Jannah a ranta bazata iya barin ta auri waniba bayan daddynta takeso dan haka duk kanta baya komai daidai kawai Daddyn ya auri jannah din. Gangarowa hawayenta sukai wanda na daddynta zai hada kaunarta da wani ne sai kuma kaunar datake wa jan sune suke fada a zuciyarta. Kuka kawai ta fasa wanda ya sakasa ajiye spoon din hannunsa batareda ta juyo ya kalletaba sbd nauyin da kirjinsa ya qara akan maganarta da kukanta dayake shiga kunnensa. Yana ajiye spoon dinsa Sayd ma duk suka ajiye nasu sbd yanayin ya sake daukan zafi. Kuka takeyi sosai mara sauti sosai wanda ciwo ne takeji a ranta amma amincewansa kila ta rage mata ciwon datakejin. Hannu ya miqa ya zari tissue ya goge bakinsa tareda miqewa yabar gurin sbd zuciyarsa zata iya riqe komai na duniya bazata iya riqe sauraron sautin kukantaba. Miqewa Sayd yayi yabi bayansa yana zarar tissue shima ya goge baki. Suna ficewa mama dawo da kallanta tayi kan falaq din dake kuka sosai wanda kwata kwata rayuwartama batasan kukan damuwaba indai ba kafin ta girmaba datake kukan daddynta idan yayi tafiya. Fiddausi ce ta shigo tana rarrashinta tareda lallabata taci abinci amma taqi ci sam. Mama ma lallabata tayi sosai akan taci din ai zai aura jannah din insha Allah dan itama tanason jannah sosai a matsayin sirikarta. Miqewa tayi tabar dining din tana kuka sosai tana cewa gurin Jannah zata. Mama na jin hakan ta kalli Fiddausi dake kokarin bin bayanta tace "Shirya kuje tinda tace zata gurin jannah din kila ta samu acan ta rarrasheta taci abinci, Ku tabbata taci kada abarta da yinwa" Gyada kai Fiddausi tayi tana bin bayan falaq din da sauri tana ambatar sunanta cikeda tsananin kulawa da kauna. Fitowa tayi bayan ta sako mini hijab akan riga da skirt din tsadaddiyar atampar datake jikinta. Fiddausi daman doguwar riga ce a jikinta ta abaya me kyau da hula dan haka dakinta ta nufa da sauri ta dauko veil din rigar ta fito tabi bayanta. Sayd dayake tareda AZIZ a palonsa ya kasa cewa komai kiran latif ne ya shigo wayarsa yana dauka latif din yace "Ga Ms Falaq Aziz nan tace zaa kaita zaadens,a tafi din? Da izinin Sir LIMBA?? Kallan AZIZ din sayd yayi yana bude baki a tausashe da girmamawa zai sanar masa AZIZ din dayaji abinda aka fada dakatar da sayd din yayi da alamar a kaita sbd tashin hankali zataita yi idan aka hanata taxo ta samu wani ciwon. Mayar da wayar kunnensa sayd yayi yacewa latif "A kaita amma kada takai dare a dawo dasu" "Ok insha Allah" Shiga motar yayi ya tada aka bude musu gate suka fice daga gidan zuwa zaadens. Koda suka isa a zadeens komai ya fara daukan zafi sbd a daidai wannna lokacin Dad ya kira jannah palonsa daga shi sai ita cikeda kulawa ya zaunar da ita kusa dashi ya dafa hannunta cikin kulawa yana kallan yanayinta na sanyi da rasa walwala da duk tayi. Karyewa zuciyarsa tayi yana jin jarabawansa shi kam akan 'yarsa ce, Allah ya riga ya jarabcesa da mata kaunar datafi komai, Akan farin cikinta da bata kulawa da inganta rayuwanta babu abinda bazai iyaba, Itace babban weakness na rayuwarsa data ahalinsa gaba daya, Ko mahaifiyar data haifeta idan zama da itane rashin walwalan yarsa tabbas zai iya sallamarta batareda second tinaniba bare aura mata wanda zuciyarta bashi takewa son aure b da qarasa rayuwarta sedai kuma bayajin zai iya barinta aure a wani gurin me nisa ko a cikin familyn da basu dace da rayuwartaba sbd itace hasken idaniyar ahalinta dan haka duk inda zataje aure sai inda zaa tattalata kaman yanda ake tattalinta a gidansu ga kuma yanayi na zuciyarta dayake jin tsoron aurenta wani gurin a sakata bacin ran da zata iya samun matsala dan haka a wani bangaren kwata kwata baya kaunar ta auri wani wanda ba Ammar dinba sbd zasu cigaba da zama a cikinsu ne. Dago idanuwanta tai itama ta kalli dad din wanda yake tinani kafin ya bude baki a natse cikin kulawa yace "Jan Zad karki boyewa Dad dinki komai, Banda kowane irin kwanciyar hankalin dayakai na ganinki a cikin farin ciki da walwalwa tareda samun kwnaciyar hankali, Karki manta you are my one and only princess, My beautiful and brave girl, Remember you don't hide anything from your dad tin kina qarama right?? Gyada kai tayi jikinta na tsananin sanyi Yace "Jannah kinason auren Ammar kokuwa kina buqatan a baki time ki sake tinani?? Kina sonsa ne kawai as brother bakya masa soyayyar aure??" Wani irin nauyin gaske dayake danne da kirjinta tsawon lokaci taji yana warwarewa ahankali idanuwanta na cikowa da hawaye sbd kunyar Dad din data kanta akan Zamowant kaman butulu ga soyayyar Ammar data taso a cikinta. Gangarowa hawayenta sukai tana rufe idanuwanta tana jin soyayyar wanda baimasan tanayi ba mai karfi da ciwon gaske, Ta laluba,ta shiga tinani,tayi kukan tayi binciken inda soyayyar Ammar ta bace bat a zuciyarta ta rasa ya akai... Sanyi jikin dad yayi sbd kenan dai ta tabbata da gaske ne ba son auren Ammar din takeba. Wani sarawa yaji kansa yayi sbd wannan wata sabuwar qaramar masifa ce zata qullu dan tabbas Ammar zai tabu,hakama shi bazai iya barinta aure wani gurinba sedai zaman gidan kenan dan bazai bari taje auren wani guri ba tinda ba lafiyayya bace a kashe masa ita a banza dan haka yaya kenan. Maheer ne ya shiga tareda rufe kofar palon yana kallan Jannah din dake kuka mai tsima zuciya sosai kan qasa ta kasa kallan dad din sbd kunyar itace take tsananin son wanda ko a jerin mutane bai gama ajiyetaba take ganin. Zaunawa Maheer yayi gefenta yana tausasa murya yace "Da gasken kenan bakyason auren?? Meyasa Jan? Ammar tin kina fadowa duniya yake miki tsananin so, Meyasa duk wannan shekarun baki bawa zuciyanki daman sonsa ba sai yanzu da komai yazo qarshe zaa muku aure?? Girgiza kai tayi cikin tsananin takaicin kanta da sanyin jikin da batasan itama ya zataiba tace "Bansaniba,wlh inasonsa ina sonsa sosai inason aurensa bansan meya sameniba yanzu, Bansan meyasa ba, Zan auresa bazan iya kasa aurensaba sbd inason nasosa kaman yanda yakeso na amma zuciyana ta kasa hakan, Kallan dad tayi wanda jikinsa ya qarasa mutuwa tace "Dad zan auresa, Shi zan aura bazan taba iya fasa aurensa ba dan Allah kada abari yasan laifin da zuciyana tai masa na kasa saka sonsa a cikinta duk da a baya nasan shine yake cikin zuciyata shi kadai..... Katse Maheer yayi da cewa "Idan a baya kina sonsa meya faru da yanzu din Jan?? AZIZ LIMBA ne???? Rintse idanuwanta tayi da karfi hawayen cikinsu na sake gangarowa ta zame qasa tana cusa kanta cikin qafafunta tana kasa cewa komai sbd abin daman ya isheta ita kadai take neman bugawa batareda fidda maganar ciki da zuciyarta ba. Dad kuwa da sauri ya kalli Maheer lafin ya kalli jannah din wadda ta sakasa sake shiga tsananin shock yace "LIMBA kuma? Shi takeso? Are they inlove with each other ko me? Numfashi me zafin gaske Maheer ya sauke yana cewa "I dont know Dad amma shine wanda take tsananin so a yanzu" Wani dan tari dad yayi yana jin tension da kuma sassaucin komai duk a lokaci daya sbd Indai har bata son auren Ammar to baida baqin cikin bawa AZIZ LIMBA jannah dinsa sbd zata cigab da samun rayuwar data taso a cikinta hankali kwance cikin kulawa me tsanani to amma AZIZ din yanason Jannah dinne shima kokuwa. Maheer ma tinanin ya shiga hakama jannah din wadda takejin nauyin zuciyarta n raguwa sbd kaman ta rage zancen zuciyanta ne ta samu sassauci. #MAMUH ZAFAFA BIYAR KALBIM 500 mamuhgee A DUNIYATA 500 Huguma AJIYA A DUHU 500 Billyn Abdul KIRJIN ME HANKALI 500 Miss xoxo Pay at 0022419171 AccessBank Maryam sani gummi Shedan biya 09033181070 Or mtn vtu at 09032345899*_KALBIM_* _Mamuhgee_ 54 Kasa cewa komai dad yayi sbd bayason ya zafafawa Jannah kuka da damuwanta sedai kuma tinda tariga ta furta da gaske zuciyarta ba son aure takewa Ammar ba tabbas bazai mata dole ba, AZIZ LIMBA kuma datake so tamkar abu ne me sauki tinda sun zama daya zai basa aurenta dan farin cikinta da kuma sake samun damar zamowa cikakken family. Maheer kuwa jin yayi kaman kuskure ne babba a cikin abinda duk yake shirin biyowa baya sedai kuma shima indai Jannah batason abu bazai iya bari a mata dolenba dan haka shima yanajin bawa AZIZ LIMBA auren Jannah Zad shine abu mafi nutsuwa a cikin lamarin. Jannah na fitowa daga gurin dad dinta falaq suna shigowa gidan. Jannah na ganin falaq din tai kokarin daidaita kanta tana sake murmushi me kyau tana cewa "Meya sameki? Meyasa take kuka Fiddausi? Shigewa jikinta falaq din tayi tana cewa "Daddy ne" Jannah na jin hakan ta kama hannunta suna nufar dakinta ta zaunar da ita ta zaro tissue tana goge mata hawayenta cikin kulawa tana cewa "Kuka bai kamaci wannan beautiful eyes din na falaq Aziz ba" Dago idanuwa falaq din tai ta zubawa jannah din wadda nata idanuwan itama suka nuna kuka tayi sosai. Hannu takai ta taba idon jannah din daya tana cewa "Jan kinyi kuka kema?? Bakyason Auren kowa sai Daddyna da gaske?? Dagowa jannah tayi ta kalleta cikin mamaki da kunyar kanta batareda ta iya cewa komaiba. "Jan nima banason ki auri kowa sai Daddy na, Inason ki zama mamana ba matar babana ba, Inason Daddyna ya aureki kada ki aura kowa kinji" Girgiza kai jannah tayi tana cewa "No falaq, i can't" cikin sanyi da mutuwar jiki. "No jan tinda kinason Daddyna kuma kina sona nai miki alkawarin sai Daddy na ya aureki insha Allah indai yanason farin cikina zai aureki a date din aurenki da Ammar Zad" Fiddausi dake zaune saurin kallan falaq din tayi dan kuwa indai ta dage da gaske to tabbas auren zai iya tabbata. Jannah kuwa Girgiza kai ta ringi yi tana cewa falaq din ta dena fadan komai na maganar manya. Falaq ce ta koma tana rarrashi da kwantarwa da jannah hankali sbd duk da tana yarinya ta fahimci wani irin so ne me karfin gaske jannah kewa Daddynta dan haka tabbas jannah zata zama matar daddynta insha Allah. Jannah din bayan ta samu ta dawo daidai itama lallaba falaq din tai taci abinci wanda tare sukaci Mimi nata tarairayansu su duka biyun sbd falaq tace ta bata na daddynta amma na iya yau ne. Anny ma sai lallaba falaq din take tana sake shige mata sbd ta gama sanin sbd falaq zata iya samun abinda yafi wanda take samu daga limbas. Sai dare suka dawo gida lokacin AZIZ na zaune palonsa har lokacin yana jiran dawowansu. Yana jin shigowansu ya sauke numfashi me sanyi yana miqewa ya shige bedroom dinsa yana nufar toilet dan wanka da shirin bacci. Hankali kwance falaq tayi bacci sbd kaman ba itace me kuka ba ta fita. Da sassafe ta tashi yau tai wanka ta shirya ta nufi bangaren Daddynta cikeda kewansa. Tana shiga shima yana palo ya gamo geam kenan ya zauna yana amsa wayar maheer dake sanar dashi family dinner da zasuyi a zadeens suna gayyatansa da familyn duka. Falaq na shigowa da gudu tayo kansa tana cewa "Daddy Goodmorning" Kashe wayarsa yayi ya Jiye yana kallan yanda take farin ciki take yaji sanyi da nutsuwan zuciyarsa sun dawo da suka dauke tin jiya. "Morning Besty, kin dena kukan?? Murmushi tayi tana cewa "Na dena,Jan tace my eyes are too cute and beautiful da basa kyau da kuka" Kallanta yayi yana sauya zancen da cewa "Zaki koma Greece da karatun ki ko kaman zaifi nan" Tashi tayi daga jikinsa da sauri tana cewa "Nooooo,bazan je koina ba, Inda kake zan zauna bazan taba zuwa koina ba dakaiba" Bai kalleta ba yace "Anan ba karatun zaki maida hankali kiyiba zakita yawone kina biyewa dumb mutane" Dariya tayi sbd tasan da jannah yake tace "No dad my jan is very brave and calm inason zama da ita itama so inason dukanku na zauna tareda ku dan haka am not going anywhere" Jin ta sako zancen da bayason yace taje gashinan fitowa breakfast. Miqewa yayi ya nufi bedroom dins ya shige toilet. Ita kuma fitowa tayi ta nufi dakin mama ta zauna tana fadawa mama ita fa dai daddynta ya auro mata Jan ta dawo gidan nan. Mama da zancen yake sake mata dadi sbd fatanta dayake neman zama gaskia na ganin aurensa. Karfe 9 ya fito a shirye cikin Sky blue tsadaddiyar yadin data kwana jikinsa da hula sai qamshinsa ke tashi yana gauraya hanyar dayake wucewa. Dining ya nufa suna zaune suna jiransa. Zaunawa yayi yana gaida mama. Suna fara cin abinci Falaq ta sake jeho masa maganar auren Jannah wanda ya sake gurbata yanayinsa amma baice komaiba yaci gaba da cin abincinsa cikin nutsuwa harya gama ya miqe ya fice. Office suka fice yana fita falaq jikinta yayi sanyi ta wuce daki tai kwanciyarta. Bata sake fitowa ba saida lokacin tafiyanta islamiyya yayi ta fito tareda Fiddausi suka shiga mota aka kaita daman da Fiddausi take zuwa sbd bai yadda koina tana zuwa ita kadaiba. Da driver da Fiddausi a mota suke jirant har tashi su dawo gida. Gabaki daya ta sauya ta bata ranta taqiwa kowa magana sbd ganin da gaske Daddynta ko maganar yaki taba cewa komai dik tai magana baya cewa komai gashi kwanakin auren sai qara matsowa suke dan haka duk tabi ta shiga damuwa me tsananin gaske sbd yanayin jannah duk da tana kokarin boyewa ta nuna komai lafiya ne sbd tana cusawa kanta son Ammar din karfi da yaji sbd ganin yanda farin cikinsa yake a bayyane jin yake kaf rayuwarsa wannan lokacin ne best lokaci na rayuwarsa sbd mallakar jannah shine hasken rayuwarsa. Mimi da batasan meyake faruwa ba da gaske take hidiman bikin wanda tini iv masu tsadar gaske wanda Anny ce ta bada aikinsi dan haka bata saka Sunan Ammar ba kawai anyisa ne a matsayin bikin Auren Jannah Zad. Mimi bata damu ba haka shima Ammar din sbd bana daurin aure bane na daurin auren tini akayosu daga Germany suna aje. Dad da maheer sosai sukeson ganin AZIZ wanda yana sane da abinda zasu fada mada dan haka yaqi basu daman haduwa dashi koyaushe baya zama sbd har cikin rantsa jin sunanta kadai qona jininsa yake bare aurenta wanda falaq ke kokarin tayar da ciwonta sbd hakan, Hakama suma sosai sike son ganinsa akan hakan... Tako wace hanya zaibi dan ganin ya hanawa Ammar samun abinda yakeso indai harya tabbata shine likitan daya cire zuciyar Ummitah da hannunsa ya saka a kirjin Jannah to amma bai taba kawowa kansa wannan hukuncin zai sakasa hada sunansa dana Zaadens ba a matsayin ahali. Falaq ta dena walwala gaba daya ta dena cin abinci sosai ta daga hankalinta wanda duk yana sane amma abinda takeso tamkar cutatarwane gareta tasowa a hannun wadda aka dauke ran mahifiyar data haifeta sbd ita. Mama ma sosai ta bude masa wutar fada da nuna bacin ranta tinda dai sun riga sun rada jannah wadda aka saka lalle dole ya nemo mata yayi aure ta basa nan da wata daya idan har ita uwarsa. Daurewa kansa yayi da damuwa kashi kashi akan lamarin musamman kalaman mama da bata taba furta masa ba hakama falaq ciwo take kokarin kwantawa sbd dumuwan data saka a ranta yana barazana ga ciwonta dan haka ajiyar zuciya ya sauke ahankali tareda kallan Sayd d komai ya gama shirywa na zuwansu Zaadens yau. Biki akeyi sosai a zadeens wanda duk Mimi ce take hidimar kowa ya lafe yaqi shiga hidimar sosai daga Mimi sai Saleem da Ammar din da amaryan kanta data dage ta sakawa kanta karfin hali bikinta takeyi sosai ko hakan zai mantar da ita komai, A yanzu tafi Ammar tsananin matsuwa da a daura musu auren sbd aure kadai zaa daura mata ta iya cire AZIZ LIMBA a zuciyarta. *****koda suka iso gidan bayan magrib ne dan haka cikin farin ciki aka tarbesu. Mimi farin cikin ganinsu tayi sbd tinda aka fara hidimar bikin basu tahoba sai yau da ake maganar daura aure washe gari. Falaq da batada lafiya sosai lafewa tayi jikin jannah tana jin tsananin kewanta da jin kaman ta dauketa su gudu d ita zuwa gidansu. Ita kanta Jannah tai kewanta sosai dan haka ta ringa tarairayanta. Falaq zuba mata idanuwa kawai takeyi tana kallan wani irin kyau da gyaran datasha ta sauya komai nata daukan ido yakeyi, Fatarta sheqi takeyi tana fidda wani irin qamshim oud da bata taba jinsa ba take taji tana tsananin kishin Ammar da tsanarsa me karfi sbd Jannah matar da zata kawo farin ciki da walwalwa a rayuwan daddynta ne sbd bayada walwala da sakewa da cikakkiyar farin ciki a Rayuwarsa tinda ya rasa mamanta dan haka jannah matar mahaifinta ce. #MAMUH ZAFAFA BIYAR KALBIM 500 mamuhgee A DUNIYATA 500 Huguma AJIYA A DUHU 500 Billyn Abdul KIRJIN ME HANKALI 500 Miss xoxo Pay at 0022419171 AccessBank Maryam sani gummi Shedan biya 09033181070 Or mtn vtu at 09032345899*_KALBIM_* _Mamuhgee_ 55 Acan palo kuwa AZIZ dinne da dad d maheer Ammar baya nan. Kallansa dad yayi yana kasa riqe abinda yake ransa, A matsayinsa na mahaifin da zai iya zubar da mutuncinsa akan yarsa indai zata samu farin ciki baya duba komai da kowa dan haka ya ajiye maganar auren da zaa daura a goben nata yace "LIMBA a matsayina na uba ina maka tayin auren 'yata sbd son da kukewa junanku..... Kallansa AZIZ ya juyo yayi yana bayyanar da mamakinsa kadan yace "Kanada wata 'yar ne? Ban taba son kowace mace ba a duniya bayan mahaifiyata d mahaifiyar Falaq sai mama da falaq, Su kadaine matan da AZIZ LIMBA ya taba so yake kuma so, So bansan wace 'yar kake magana ba coz i thought you only had one daughter wadda zaa daurawa aure gobe." Kallan Maheer yayi lokacin dayake qarasa maganarsa alaman ko akwai wata yar? Wani rikitaccen numfashi dad ya sauke hakama maheer rasa abin fada yayi sbd basu taba sanin akwai wanda zai iya fadar magana kai tsaye haka ba akan fuskansu. Rikicewa maheer yayi zuciyarsa na tsananin zafi da baqin cikin cin fuskan da maganar AZIZ din dan haka ya bude baki zaiyi magana Dad da jininsa yake dan hawa ya dakatar dashi sbd basuda zabin daya wuce daidaitawa dashi ya karbi auren rinda jannah na tsananin sonsa kafin gobe farin cikinta ya lalace idan ta rasashi gaba daya. Daidaita kai dad yayi cikin nutsuwa da nuna mahimmancin zancen yace "Duk da hakan ni a matsayina na ubanta na baka aurenta idan har zaka amsa sbd kaunar datake tsakaninmu" Dan gajeran murmushi me kyau da nutsuwa ya sake kai tsaye cikin steez yace "No,thank you" Wani irin zufa ne ya tsinkowa dad din yana kallan AZIZ din wanda kai tsaye yake maganarsa hankali kwance ba kawaici ko daya. Maheer kuwa kirjinsa yaji ya toshe y kasa furta komai. Qamshin jannah dinne me shegen dadi da nutsuwa yafara shigowa palon kafin ta sako kai palon cikin riga da skirt na wani plain lace mara nauyi d tsada ya zauna daidai jikinta komai nata ya fito d kyau. Batasan yana palon ba dan haka ko dankwali babu a kanta dayake daure amma y dan yamutse kadin sbd falaq dake shafa mata shi tin dazu. Magana zatai idanuwanta suka sauka akansa daidai lokacin shima ya dago amma sam idanuwansa basu sauka akanta ba wayarsa ya daga. Cak maganarta ta dauke kirjinta ya buga da karfi ta kasa cewa komai saidata hadiye wani nauyin kirji kafin ta bude baki tace "Dinner Dad" Gyada mata kai yayi sbd shima ya kasa iya maganar. Miqewa dad din yayi yayi gaba jikinsa duk a mace sbd sedai a daga daurin auren nan zuwa gaba amma bazaa iya daurasa ba tausayin yarsa yakeji sbd ko yanzu shi kadai yasan meya gani a idanuwanta lokacinda taga AZIZ din. Maheer dayake jin yan suffocating da sauri ya wuce dad ya fice dad na bayansa. Itace a bayansu tana kokarin bin bayansu ba tsammani abinda bata taba jib taji an riqo hannunta ta baya. Cak zuciyarta da dena bugawa numfashinta na kokarin daukewa sbd tsananin shock da mamaki. Kasa juyowa tayi sbd gap take da samun attack sbd qamshinsa dayake shiga hancinta direct daga jikinsa. Attack yakeson bata sbd bayason barin gidan ayau sai yasan waye asalin likitan dasuke son sani sbd idan ba sauri yayiba aikinsa zai dade akansu gashi plans na sauyawa aurenta yana neman shigowa ciki bayan babu wannan banzan tsarin ko kadan a cikin plans nasa dan haka samun attack dinta a yanzu shine daidai lokacinda ya kamata ya san abinda yakeson sani. Juyowa yayi da ita suna fuskantar juna a zuba mata idanuwansa tareda yiwa hannunta wani irin riqon daya saka zuciyarta kasa riqe bugawan ta dago idanuwanta ta zuba masa take taji tana samun attack ta zube a gurin. Tsallaketa yayi ya fice daga palon daidai nan falaq tazo kiranta kafin tace masa komai ta hango jannah a qasa zube tana neman numfashinta dayake kakarin barin jikinta d qarfi ta kira sunant wanda ya saka kowa dawowa da sauri anayi kan Jannah din cikin matsanancin tashin hankali. Dad da maheer ne alokacin daya sukacewa Mimi "Ina Ammar ayi sauri a kirasa da gaggawa...." Mimi ma cikin tashin hankalin ta saka kiran wayarsa tana cewa "Ammar kayi sauri jannah is having an attack " AZIZ da Sayd da sukai mutuwar tsaye suna jiran zuwan Ammar din wanda yazo da mugun sauri daman yana cikin gidan dawowansa kenan yana harabar gidan. Yana shigowa da sauri ya dauketa cak ya kwantar a kujeran palon ya miqa hannuwansa biyu duka zai bude rigarta dan fara duba bugun zuciyarta aka riqe hannuwan nasa duka biyu cak. Da wani irin tsananin mamaki da tashin hankali ya juyo. Sayd ne y riqe hannuwansa yana kallansa. Kusan kowa dauke wuta yayi a gurin sbd mamaki da tashin hankalin halinda jannah din ke ciki. AZIZ ne ya tako a hankali cikin isa ya tsaya gaban dad ya kallesa yace "Idan nace na karba auren daka bani nata kana ganin ya dace shi wannan din ya bude jikinta anan ya tabata? Dan haka bazai tabataba a nemo likita, Yana dora hannunsa akanta bazan taba aurentaba har abada." Cikin wani irin mummunan tashin hankali da shock Ammar ya kalli AZIZ din mimi ma shock din t shiga da tashin hankalin tana kallansa hankali kwance yayi maganar babu damuwar komai aransa dan badan zuciyar dake bugawa a kirjinta ba bazaiqi ta buga a yanzu ta mutu a gurinba. Sayd sakin hannuwan Ammar yayi yana matsawa baya. Cikin tsananin fushi da kansa dayake neman juyewa Ammar ya miqa hannunsa zau bude rigar Maheer ya riqe hannunsa da sauri yana Girgiza masai. Dad kuwa cikin jininsa dayake neman hayewa cikin damuwa me tsanani ya kalli AZIZ yace "Likatane shi kansa din Dr Ammar Zad Shine likitanta tin b yanzu ba zai dubata ne a matsayin likita ba wani abinba daban........ Dago idanuwansa yayi ya zubawa dad din sbd daga karshe dai sun fada abinda yakeson tabbatarwa. Ammar din ya yiwa wani kallan daya saka Mimi zubewa zaune sbd jirim dayake dibanta. Irin kallan da yayiwa Ammar shi ya yiwa dad da maheer kafin ya hadiye wutar dake cin zuciyarsa ya bude baki yace "Na karba sadakarka a goben zan aureta a matsayin uwar da Falaq takeso" Juyawa yayi yabar palon sayd ya kama hannun falaq dake riqe dana jannah din suka bi bayansa daman mama na can palon take Fiddausi na ganin fitowarsu ta kirata suka bar gidan AZIZ din da kansa yace mata ta shirya gobe zaa daura masa auren datake so. A cikin palon Kuwa wani masifaffen tension ne me karfim gaske ya cike gurin sbd Ammar kasa motsawa yayi idanuwansa akan maheer dayake riqe da hannuwansa. Mimi kuwa jin tayi numfashinta yana neman daukewa itama Dad dinma jininsa sama ya ringa yi yana kasa kallan Ammar sbd bai san AZIZ zaiyi magana a gaban Ammar din ba. #MAMUH*_KALBIM_* _Mamuhgee_ 56 Falaq farin cikine ya ciketa gabaki daya na jin Daddynta zai aura Jannah dan haka a mota qanqame hannunsa tayi tana bayyanar da farin cikinta ta kalli fuskansa da babu alamar farin ciki ko kadan a kanta tace "I love you Daddy" Juyowa yayi a hankali cikin nutsuwa ya saukar da idanuwansa akanta yana karantar asalin farin cikin me tsanani dayake bayyane akan fuskanta tana murmushi tana jin kaman tin yau ta tafi da jannah din gidansu. Sayd dayake gaba shiru yayi yana sauraransu ta wani bangaren kuma shima hakan shine abinda yake tsananin so wato rabo zuciyar Ummitah daga zaadens sbd kada ta gurbata kaman yanda duka zuciyar familyn take a gurbace, Babban fatarsa kafin su illata familyn ya zama zuciyar Ummitah tana tareda su dan haka shi wannan hukuncin shine daidai garesa kuma abinda yake jira dan haka daga lokacinda akai auren ta gama shigowa hannunsu komai ya nutsu to lokacin tarwatsa familyn zai fara duk da suna nan suna tsananin neman Dr ken wanda shi sukeson ya shiga hannunsa kafin komai sbd shine ya basu Ummitah, Sunason Farawa Dasu dr Abraham amma kuma dole saisun fara kama dr ken sbd shine komai ya fito ta hannunsa dan haka nemansa suke sosai saidashi komai zai tafi yanda akeso. Mama kuwa jin tayi zuciyarta kaman ta zuba ruwa a qasa tasha dan haka koda suka isa gida kasa shirin bacci tayi ta zauna tahau wayoyi. Anty maryam ta fara kira akan lefen datakeson a hada mata na gani na fada a qanqanin lokaci. Anty maryam na jin maganar auren farin ciki me tsanani da mamaki me girma suka rufeta lokaci daya da kuma Acikin yayanta dataita kwadayin ya auri daya amma duk da hakan farin ciki sosai tayi ta matsu goben tayi su isa LIMBAs din. Baba alhassan ma daman yana nan har lokacin dan hana mama na sanar masa Sayd ya kira yaji komai daga bakinsa sbd AZIZ din ya shige ya hana kowa sake ganinsa sbd tsananin zafin kansa dayakeji yana jin kaman hakan bai kamata ba ga UMMITANSA to amma yana tsananin buqatan zuciyar Ummitah a kusa dashi. Ruwa ne ya sakarwa kansa batareda ya cire kayan jikinsa idanuwansa a rufe ya qanqame jikinsa yanajin kaman kansa zai juye sbd tsananin zafin dayake tashi a cikinsa, Yana tsananin qin Zaadens da jannah din kanta tsana me tsananin gaske da zai iya komai dan faduwarsu koda hakan na nufin su fadi tare, Ta bagare daya yana tsananin Kaunar duk abinda ya shafi Ummitah koda qazantace indai ta Ummitah ce sonta yake da gaske, Baitaba qi ko gudun abinda ya shafi Ummitah ba, Ta bar duniya bazata taba dawowa har abada amma zuciyarta na duniya taba bugawa tayaya zai tsani kirjin da zuciyar Ummitah take bugawa a cikinta???? Zuciyarsa ta kasa hakan, Ya tsani jannah tsana mafi muni a lokaci day kuma yana tsananin kaunar zuciyar datake bugawa a kirjinta.... Rawa jikinsa yakeyi sosai yana wani irin jijjiga yana sake qanqame jikinsa da karfi sbd trauma dinsa da shima babu lokacinda bata tashi idan ya samu kansa a cikin wannan tsananin ciwo da radadin tinanin kauna da tsana dake cinsa lokaci daya wanda babu wanda ya taba sanin da hakan. Ruwan sosai sike sauka jikinsa jikin nasa na sake daukan jijjiga idanuwansa sunyi wani irin jan da idan da wani zaigansa a lokacin tsoro zaiji. Azaba ce sosai yake ji a cikin kansa yafara buga kan a jikin bango da karfi kafin qafafunsa suka kasa riqesa ya silale a gurin qasa yana qanqame jikinsa har lokacin ruwa na sauka akansa. Tsawon lokaci yana matse da jikinsa qasa kwance jikinsa na rawa sosai ruwa na sauka akansa ahankali ahankali harya nutsu yayi shiru idanuwansa a rufe wasu hawaye masu tsananin zafi suna gangarowa daga idanuwansa ya budesu ahankali yana ganin kamar Ummitansa na gabansa ya qurawa gabansa ido kaman itada mahaifiyarsa suna tareda shi. Ya jima a hakan zuciyarsa na karairayewa kafin ya lumshe idanuwansa yana fatan duk suna cikin rahamar ubangiji. Daqyar ya iya kai hannunsa ya sauya zuwa ruwan zafi ya miqe ya zare kayansa yayi wanka da tsadaddun shower liquids dinsa kafin ya zari daya daga cikin towels din dasuke jere a toilet din masu yawa sa laushi ya daura a jikinsa ya fito fararen idanuwansa da suka sauya sunyi wani iri kaman sexy dan da akwai macen da zata gansa a lokacin tabbasa zata iya kasa riqe kanta dan kallo daya zai maka dasu ka nema zarewa da neman nutsuwarka ka rasa. Tin daga lokacinda ya Ummitah tabar duniya tabarda da wannann trauma din babu daren da baya samun kansa a wannan yanayin batareda da kowa ya taba saniba, Shi kadai yakeshan azabarsa ya gama ya fito batareda kowa y saniba sai dr Nico wanda shine likitansa, Azaba sosai yakesha sbd zuciyarsa haryanzu ta kasa fita daga radadi da ciwon rashin yar Uwarsa wadda sai ranar daya bar Duniya zai huta daga wannan ciwon. Ko Sayd baitaba saniba sai daga baya bayan shekaru ya sani a wani tafiya da sukai ya samesa dakinsa da daddare akan wani issue ya tararda yana bathroom wani irin kuka da nishin dayake jine ya sakasa nufar bathroom din wanda ya tarar dashi a wannan halin, Tim daga wannan lokacin ya san ashe AZIZ din bai warke daga trauma dinsaba sai tsananin data qara amma tsawon shekaru basu taba saniba sbd ya zabi ya boye ya ringa jin radadinsa shi kadai. Tin daga wannan lokacin Sayd ya tsananta kaunarsa da kulawansa akan AZIZ din, A lokuta da dama shine yakan rungumesa idan yanayin yazo masa dan sassauta masa ciwon yana hawayen radadin ganinsa a cikin wannan yanayin. Dr Nico na iya kokarinsa akan hakan sbd shine therapist dinsa dan haka sauki yake samu sosai ana samun cigaba sosai sai gashi kwatsam Maganar kashe Ummitan akai ta bayyana wanda ya dawo da komai baya dan kwata kwata yanzu ya dena karban kokarin da akeyi akan yanayin nasa. Tsananta yanayinsa yayi sbd yanda aka kashe Ummitah shine kisa mafi tsananin ciwo da rashin tausayi, Abinda yake Tsananta yanayinsa a koyaushe shine yasan Ummitah zataso inama ace Allah zai bata ikon ganinsa yazo gareta, Inama zasu tausaya mata su barta ta koma ga dan uwanta da mijinta da abinda ta haifa da mamanta, Ya sani a wannan lokacin da suke kokarin rabata da duniya tayi hawayen azaba,tayi na rashin sanin ayau zata bar duniya,tayi na tausayinsa sbd tasan zai shiga tashin hankalin da babu ranar fita... Tina irin wannan ne yake sakasa hawayen tausayin kansa dana yar uwarsa a kowane lokacin da yanayinsa ya taso. A yanzu dayakeson yi musu tsanar datafi komai karfi da muni a yanxu dinne kuma zuciyarsa ke jin tsananin kaunar Zuciyar tata datake bugawa da tsananin sonsa da kaunarsa amma a wani kirjin da bana Ummitanba, Ta tafi tabar masa bugun zuciyarta dayake tsananin son jinsa a hannunsa, Ya tsane Jannah amma yana kaunar bugun zuciyarta tayaya zai iya barin kansa ya hada wainnan feelings din guda biyu? Tsananin tsana da kuma tsananin kauna... Wannan tinanin ke sakasa tsanar kansa tsana me tsananin gaske, Amma duk da hakan bazai taba samun nutsuwa ba saiya tabbatarda Jannah bata sake dandanar farin cikin duniya ba, Zaadens suna kallo zai mayarda rayuwar da sukafi so fiyeda komai ba komaiba, Suna kallo zai maidata abar tausayi da baqin cikin kallo bazasu iya komaiba sbd sun riga sun daura aurenda bazasu iya rabawaba sai lokacinda ya gama da ita zai jefa musu ita a lokacinda batada amfanin komai a duniyar dan haka Auren a goben ba fashi ya karba sadakarta hakama ya bawa falaq abinda takeso itama mama ya cika mata umarninta na son yayi auren. Su Mama kuwa hankali kwance sukam sunga hidimar farin ciki gabansu, Baba alhassan Alh saad ya kira ya sanar masa maganar auren da babu shiri dan haka ya sanar masa goben dai sune wakilan ango. Bayan ya kira Alh saad Alh Ahmed ya kira abokin aikin Baban AZIZ din wanda shine ya kawosa gurin su Alh saad tin lokacinda mahaifinsu ya rasu. Shima sosai yayi farin ciki dan haka da shirinsa ya kwana yace shine zai biya sadaki Baba alhassan yace aa shine zai biya,shima Alh saad cewa yayi shine zai biya baba alhassan yace sam shine zai biya sadakin. Qin yadda sukai sukace aa yabari su biya, Ganin kowannensu nason ya kasance shine ya biya sadakin auren wanda sukejinsa har cikin ransu tamkar sune suka haifesa dan haka suka yadda akan kowa ya bada 500k su biya sadakin 1.5. Baba alhassan ne yace aa sbd albarkar aure baa son sadaki me yawaba 100k kowa zai bada ayi sadakin 300k ma ya isa. Amincewa sukai sa hakan dan haka kowannensu a cikin daren yafara kokarin buga wayoyin gayyatar jamaarsa da manyan mutane. A cikin daren Sayd yasa aka buga wata lafiyayyar invitation ta waya a cikin daren aka fara yadawa manyan mutanensa dake kusa harma da wanda basa kusa bazasu samu damar zuwaba sbd kurewan time amma a cikin daren kafin safe maganar Auren AZIZ AY LIMBA da JANNAH ZAD ta fita anata mamakin lamarin amma dayake already Zaadens sunyi gayyata tin kafin yanzu sai ya zama mutane da yawa da manyan kasashe da dama da zasu halarta already suna abuja sun iso a ranar sbd goben sai gashi a daren suke samun kuma AZIZ LIMBA ne wanda zaa daura dashi goben. ********** A ZADEENs kuwa AZIZ da familynsa na barin mansion din shiru sukai kowa ya kasa motsi sbd ya bude aikin da basu shirya tarbansa yanxuba. Ammar wani irin ja idanuwansa sukai yana jin kansa da tinaninsa na toshewa kasa cewa komai yayi bayani yake jira daga duk wanda Allah ya bawa ikon fara samun dawowa hayyacinsa a cikinsu sbd yasan suma shock din suke ciki na jin zancen haukan da LIMBA yayi. #MAMUH ZAFAFA BIYAR KALBIM 500 mamuhgee A DUNIYATA 500 Huguma AJIYA A DUHU 500 Billyn Abdul KIRJIN ME HANKALI 500 Miss xoxo Pay at 0022419171 AccessBank Maryam sani gummi Shedan biya 09033181070 Or mtn vtu at 09032345899*_KALBIM_* _Mamuhgee_ 57 Mimi ce ta iya bude baki dakyar zatai magana hannuwanta na rawa Anny tai saurin riqe hannuwanta da sauri cikin kulawa dan hanata maganar da zata fada tace "Mimi karkice komai,ki kwantar da hankalinki Abinda kikaji ba hakan bane muje ki samu nutsuwa sai amiki bayanin komai daga baya. Zare hannunta mimi tai daga na Anny tana kallan Maheer kafin ta maida kallanta kan Dad tace "Auren Ammar da jannah buri na ne tin daga ranar dana haifeta ta diro duniya, Bazan taba karban Kowane miji ga jannah ba bayan Ammar, Idan akwai abinda yake faruwa ku sani ban yadda dashiba Koda wasa aka fasa auran Ammar da jannah kunci Amanata da Ammar harma da jannah din" Maheer baice komaiba ya kalli Anny batareda yace komaiba ta fahimci abinda yake nufi na taja Mimin zuwa daki. Sake kama hannun Mimin tayi tana cewa "Mimi muje ki huta babu abinda zai faru insha Allah ki kwantar da hankalinki wlh bazaa aurawa jannah kowaba sai wanda takeso dan haka muje ki huta gobe ranar farin ciki ce" Dad da baice komaiba kallan Anny yayi wanda itama shi ta kalla take ta fahimci nasa Kallan itama dan haka jan Mimi tayi cikin kulawa zuwa bedroom dinta sbd sosai ta shiga tashin hankali da shock dan haka jininta ya hau sosai. Suna isa daki taimaka mata tai ta kwanta taje qaramin dakin maganin da ake dashi a mansion din sbd ciwon jannah kawai da duk sauran ciwon yan gidan duka tinda sunada nurse sunda likita shiyasa komai akwai gidan. Magani ta dauko me karfin gaske tasa a juice ta bawa Mimin cikeda kulawa tana cewa Mimi sha zaki samu dan sauki saikiyi baccin ko minti 30 kanki ya sake. Sha Mimin tayi sosai sbd maqoshinta daya bushe sbd tashin hankalin. Tana miqawa Anny cup din taji idanuwanta na juyawa kanta ma na juyawa kafin tayi wani motsin ta zube a gadon. Gyara mata kwanciya Anny tayi tana sauke ajiyar zuciya tareda rufeta tana cewa "Sorry Mimi koda zaki tashi Jannah ta jima da zama JANNAH LIMBA, Mrs AY LIMBA Daga baya kinyi bayanin Alkawarin aurenta da Ammar saiki hada da hakuri" Juyawa tayi ta fice dakin tana rufowa ta koma palon Dad dan tayasu handling Ammar sbd ba wata dubara ce dasu ba zasu iya lalata komai. Tana shigowa palon Ammar na miqewa tsaye zaiyi magana jikinsa na wata irin jijjiga sosai da sauri ta isa gurinsa tana cewa "Ba maganar komai zaayiba a fara neman lafiyan jan tukuna." Kaman dukkaninsu jira suke suka sake yi kan Jan har Ammar din wanda yake ransa kansa akan duk abinda ya shafi jannah. Jannah din ta dawo daidai numfashinta ya daidaita sedai idanuwanta a rufe suke bata iya komai. Dad ne ya kalli Maheer yace ya dauketa yakaita dakinta. Cak Maheer din ya dauketa ya fice da ita sai alokacin Ammar ya dago jajayen idanuwansa ya kalli dadi hannuwansa na tsananta rawa ya bude baki muryansa na hadewa da rawa yace "Dad what's going on? Is there something daya kamata na sani? Abin nufi Dad akwai abinda yakamata na sani?? Dad bakaji me bastard dincan ya fada bane kafin ya fita? Yana magana akan auren My jannah, My jannah,my jannah fa dad., Anny ce tayi saurin cewa "Ammar you have to calm down kafin ka fahimci abinda ake nufi, AZIZ zai auri jannah ne sbd yana son bawa yarsa uwa, Mu kuma muna tsananin buqatan dukiyarsa gabaki dayanta... Wani mahaukacin kallo yayi mata da idanuwansa dake wani irin sauyawa kaman zasubkama da wuta yace "Are kidding me? Meya hada aurena dana jannah da duk abinda kike magana? To hell with his daughter, Idanma mutuwa zatai i dont care I don't give a damn Ta mutu kawai shima ya mutu amma bazan taba bari wani yama sake furta maganar auren Jan dita ba batateda na dauki matakin illatasaba" Dad Zaunawa yayi Ahankali har lokacin baice komaiba sbd harga Allah baisan tayaya zai bullowa lamarinba sbd AZIZ ya janyo musu matsalarda bata hakan yaso bullowa Ammar dinba. Anny ce ta sake bude baki ganin koina jikin Ammar din rawa yake yana neman loosing control ya fara musu fashe fashen kaya karshe ma zai iya raunana kansa ya raunana wani tace "Ammar pls calm down" Batada zabin daya wuce shirya masa karyan da zata fiddasu dan haka kallan dad tayi kafin ta kalli Maheer dayake nufar Ammar din da tausarsa tayi saurin tare Maheer din kada yaje Ammar ya rasa control nasa ya illatasa dan haka tace "Ammar abinda yake faruwa shine Falaq Aziz nada ciwon da mutuwa zatai she only hv 3 month to live, Tana tsananin son Jan as her mum Kuma ka sani akwai kauna tsakaninsu sosai, Daddynta na son bata farin ciki a kwanakin da suka rage mata so ya roka abasa auren jannah for only 3 month shikuma zai bamu dukkanin abinda ya mallaka in return...... "What¿" Ammar ya fada cikin tsananin mamaki da sabon tashin hankali sbd zancen kadai neman sake juyar masa da kai yakeyi. Dad kuwa da sauri ya kalli Anny kansa na sarawa da tsananin ciwo shima jin abinda take fada... Magana zaiyi Maheer ya bude baki a hankali yace "Dad a tafi a hakan atlast idan ya aminta zamu samu ayi auren daga baya asan yanda zaayi" Maheer dinne ya karbi zancen d cewa "Ka sani muna cikin financial crisis hakama shine biggest catch namu da muka sani zai iya tadomu, And atlast tinda anzama kamar family bazamu iya taimaka masaba akan yarsa? Auren wata 3 fa? Idan harmu dukanmu zamu iya yadda da hakan meyasa kai bazaka iyaba, Babu wani soyayyar dayake tsakaninsu, Kana tinanin akwai abinda zai girgiza soyayyar da jannah take maka? Ita kanta zatai ne sbd falaq, Gabaki daya assets dinsa zai bayar a matsayin auren kankanin lokaci, Bazaka iya sacrificing wata uku naka ga familynka ba? Karka manta mun taso da taru a tinani daya da tabbatarda ci gabanmu, Meya canza Ammar? Kana tinanin har abada zamu taba son wani ya auri jannah akanka? Wlh muna kaunarka fiyeda yanda kake tinani ta yanda ka dauka hakan da zamuyi babu zabi ne kuka bamu yadda da hakan bane saida muka tabbatarda lokaci muka bawa auren zamu dawo da ita gareka." Ganin zancen yafara shigar Ammar ya saka Dad dago idanuwansa da suka sauya ya kalli Ammar yace "Ammar indai nine na haifi Jannah insha Allah nai maka alkawarin aure maka ita indai har zaka iya hakura a yanzu dan samarwa kanmu mafitar abinda mukeso, Ban basa aurenta dan ta zauna dashi har abada ba na basa ne sbd ita kanta Jannah din ta samu abinda takeso a can amma insha Allah zata dawo a lokacin ne zan daura muku aure da hannuna, Ka sani Ammar ina sonka sbd kai jinin Zayneb ne da har abada jinin Zeynab yafi komai dana mallaka daraja amma ayau ina rokon ka bamu lokaci kankanin a cikin soyayyar da kakewa Jannah" Wasu irin hawayen masu tsananin radadi da baisan suna fito masa bane suka fara gangarowa Ammar din kafafunsa na wata irin rawa zuciyarsa na neman bugawa ya zube gurin jikinsa na rawa ya fara girgiza kai yana cewa "No,no i can't" Har abada bazan iya kallan jannah a hannun wani ba koda na minti dayane bare wata uku, Bazan iyaba dad Mutuwa zanyi, Zuciyata bugawa zatai, Dad bazan iya ba, Mutuwa zanyi" Kirjinsa ya dafe yana masa wani irin tsananin radadi da azaba kansa na neman juye masa yana jijjiga yafara daga murya sosai yana cewa bazai iyaba mutuwa zaiyi, Indai aka aurawa jannah wani zai iya kashesa ya rabasa da duniya koma waye. Anny na ganin hakan ta kalli su Dad tace "He's looking it,inaga ai masa Allura ya samu bacci idan ya tashi kansa ya sake zaifi fahimtar abinda ake nufi amma a yanzu yana rikicewa komai zai dagule" Kallanta dad yayi yace tai masa alluran kawai sbd yana rikicewan nan raunana kansa zaiyi wanda ya tsani ganinsa a cikin yanayin da zai raunana kansa dan harga Allah tin daga zuciyarsa kaunar Ammar take amma kuka bazai iyawa jannah auren da bataso ba wanda hakan zai iya kawo matsala a cikinsu dan daman tin farko sbd basason matsala ta shigo tsakaninsu sbd tsananin kaunar da sukewa juna basa wani son auren zumucin amma kuma sbd dagewan Mimi da ganin yanda Jannah din take tsananin son Ammar da yanda yake mutuwar sonta suka kaunace auren harya sabu da jin bazai iya kaita aure wani gurin ba bayan na nan cikin gida. Kafin suyi wani yunkuri Ammar din ya fara haukace musu da sauri Maheer ya rungumesa yana kokarin calming dinsa amma ina dan haka dole Anny tai masa allurar da baisan da itaba kuma batareda sanin kowa ba high dose ta basa dan haka bedroom dinsa Maheer yakaisa y kwantR tareda rufesa ya daidaita masa ac bayan ya sauya masa kayansa zuwa na bacci marasa nauyi dan haka baccin kwanciyar hankali suka sakasa. Anny jin tai hankalinta ya kwanta dan daga Mimi har Ammar din insha Allah sai gama daurin aure zasu tashi dan haka itace ta karbi ragamar hidiman bikin cikeda farin ciki. Dad da wuri ya shige zuciyarsa na shiga wani irin rashin nutsuwa haka kawai ga jininsa daya dan hau dan haka yasha magani ya shige. Kiran Alh saad ne ya shigo wayarsa suka gaisa ya bayyanar masa da matsayinsa na wakilin AZIZ suka dan tattauna akan goben kafin sukai sallama. Maheer ma damuwar yakejin ya shiga haka kawai sbd jin kaman abind yake faruwa bai kamata ba amma Anny ta dage ta sakasa dawowa da mood dinsa daidai. ********Washe gari tinda safe Su Baba alhassan da Alh Ahmed da Alh saad suka taho gidan suka sake gabatar da kansu sukai neman aure yanda ya kamata tareda kudin neman Aure ten mil suka baro sai kuma sun hade gurin daurin auren karfe goma sha biyu na ranar. Saleem daya kasa yadda da cewan Jannah AZIZ takeso saida yayi magana da ita ya tabbatarda da hakan dan haka shima bai wani daga hankalinsa ba duk da su dad basu bude masa zancen sosaiba dan haka koda akace damuwa ta saka su Mimi fitowa sai bai takura Mimin ba tinda ya shiga ya sameta tana bacci hankali kwance hakama Ammar din dan haka kai tsaye cikin farin ciki yahau shirin daurin auren mutane biyu dayake tsananin kauna. Jannah kasa Fitowa tayi duk da gidan akwai mutane rufe kanta tayi a daki tana kasa fitowa duk da batasan meyake faruwaba dan taqi barin kowa ya shigo mata hakama ta kashe wayarta hakama jamaar bikin basusan shaanin da ake cikinsaba hidima kawai Ake Anny kaman zata tashi sama sbd farin ciki. Yau ranar aurenta da Ammar amma ayau din zata rasa farin cikin zuciyarta har abada dan haka zuciyarta take cikin wani irin yanayi na sanyi da rashin kuzari ko kadan dan hakanne ta kasa barin kowa ya ganta har lokacin daurin auren yayi. Cikin shegun motocin dake Zaaden masu tsadar gaske da tarin securities su Dad suka fito zuwa daurin auren harda Daddy Mahmoud wanda yake cikin wasu shegun kaya masu tsadar gaske da sandarsa dayake takawa ahankali dan ya fara takawa. Kowannensu asalin dukiyace a jikinsu tin daga manyan kayan dake jikinsu zuwa agogayensu da shoes Luxuries tako ina kawai. Koda suka isa masallacin da zaa dauka gabaki daya anguwar koina securities da jamian tsaro an cika. Su Alh saad already sun iso suma dan haka AZIZ din ake jira wanda very late ya iso. A cikin wata black RR ya iso gurin wadda ta saka aka san da shine din ya iso. Sayd ne ya fara fitowa da fahad wanda ya baifi mintina arbain da sauka Nigeria dinba. #MAMUH #TWO PSYCHOS #CRAZY Lovers #limbas #zaadens ZAFAFA BIYAR KALBIM 500 mamuhgee A DUNIYATA 500 Huguma AJIYA A DUHU 500 Billyn Abdul KIRJIN ME HANKALI 500 Miss xoxo Pay at 0022419171 AccessBank Maryam sani gummi Shedan biya 09033181070 Or mtn vtu at 09032345899*_KALBIM_* _Mamuhgee_ 58 Dad da Maheer dake jin matsuwar a daura auren suna jin sanarwan isowansa ajiyar zuciya suka sauke a tare cikin sirri sunajin nauyin kirjinsu na raguwa sbd maganace kadai basuyi da junansu ba amma babu wanda babu shakkar Zuwan AZIZ LIMBA a zuciyarsa sbd a yanda yake baa gane alkiblansa zai iya qin zuwa ko cewa bai karba aurenba wanda a daidai wannan lokacin idan yayi hakan ayau sun gama saukowa daga zaadens a idon mutane sun koma dezaans kila dan haka duk murmushi da farin cikin dayake bayyane a fuskokinsu fargaba da rashin nutsuwa ne a fuskokinsu saida sukaji isowansa suka saukin abinda ya toshe kirjinsu. Fitowa yayi mota sanye da wani black tsadaddiyar luxury cashmere datai masa wani irin kyau da hula a kansa qamshinsa kadai me kirari ya shaqa take ya sauya kirarinsa yana qarawa da me qamshin alkhairi da babu irinsa. Securities ne suke sake bawa gurin tsaro yana wucewa kai tsaye ciki Sayd na gefensa da Securities a bayansu sai fahad dayake gabansu ya basa kariya ta gaban. Suna shiga masallacin take aka fara kokarim daura auren sbd ana kokarin gota lokacin da akace. Dakatar daurin auren AZIZ din yayi lokacin da yake kokarin qarasowa har gurinsu Baba alhassan dake kokarin gabatar da komai. Wani irin kallo Maheer ya dago da sauri yanawa AZIZ din zuciyarsa na bugawa da karfi da kuma mamakin menene. Dad kuwa numfashi ya sauke ahankali yana dan lumshe idanuwansa yana jiran jin abinda AZIZ zai fada wanda zai iya sakasa samun Mummunan shock a gurin komaima zai iya faruwa dan haka kasa dagowa tayi yana jiran jin wani abin. Maheer kuwa kafe AZIZ din yayi da ido yana jiran abinda zai fada sedai idanuwansa na bayyanarda sanyinsa da tsinkewansa sosai tareda qasqantar da akai akan kada komai ya samu auren farin cikin Jannah. AZIZ saukar da idanuwansa yayi akan Dad da sadakarwansa take a bayyane cikin jiran abinda zai biyo baya, Maheer kuwa tamkar magiya ce a tsakiyar idanuwansa dake kokarin sauyawa ammma yana hana hakan bayyana. Sauke nutsatsiyar numfashi AZIZ din yayi yana samun nutsuwa daga tashin hankalin daya gansu a cikinsa batareda sun fada ko nunawaba shi ya hango sarewa da magiyar koma me zaiyi kada ya fasa auren a wannan lokacin. Bazai fara aurenba sbd shima yanada reputation dayake son karewa kawai tashin hankalinsu da tsoronsu yakeson gani shiyasa dan haka kallansu baba alhassan yayi tareda sake wani Kyakkyawar murmushi daya saka kwarjinsa cike gurin sosai yace "Bismillah Baba daman zaunawa nakeson nayi sbd na karbi igiyoyin aurena da kyau" Dariya aka sake cikeda mamakin rahar tasa sbd abace da bayayi. Daurin auren aka fara su Dad na sauke ajiyar zuciya zufa na dan tsinko masa yana tinanin babu wanda ya isa yayi musu hakan a rayuwa sai wannan me isar da zafin kan amma zasu daidaitasa ne idan suka gama samun abinda sukeso. An daura Auren na AZIZ AY LIMBA da JANNAH ZAADEN akan sadaki dubu dari uku laqadan ba ajalan ba, a bisa koyarwan maaiki, AZIZ LIMBA a yanzu shine me cikakkiyar iko kowace iri ce ta rayuwar jannah Zad.. Ajiyan zuciya da numfashi me dumi suka sauke dukkaninsu take aka fara adduar Allah ya sanya alkhairi ana tayasu murna ta koina sbd aure dai y dauru an daurasa. Baba alhassan da Alh saad har cikin ransu suke jin wani irin farin ciki da nutsuwar AZIZ din yayi Aure sbd ya dauki lokaci sosai kafin yayi auren a lokacin da basu saka rai ba dan haka kudi sosai suke fitarwa suna rabawa. DZad ma farin cikin ne me yawan gaske a ransa da kan fuskansa dan haka ya saki fuska sosai cikeda farin ciki yana amsa addua tareda godia ga manyan baqinsu manya da suka samu halartar daurin auren. LIMBA dinma mutane yake gaisawa dasu sosai sedai ba wani sakewa da zallan bayyanarda farin ciki kaman familyn zaadens da nasa. Sayd kuwa bakin Aljihu ya bude kaman bai taba sanin zafin kudi ba yace aje a rabawa maroqan dake can waje sbd karfin securities dake gurin bai basu damar shigowa ba kusa ko kadan sbd manyan mutanen da suke riqe da qasar kusan duk suna gurin shiyasa tsananin tsaron yai mugun yawa. Dayake Saturday ce daga can bayan manyan baqinsu sun rage sosai duk sun wuce suma motocinsu suka fada tareda securities nasu suka baro zuwa gida zuwa lokacin Time na sallah yayi dan haka Masallaci suka fara tsayawa dukkaninsu da tarin securities sukai Sallan Azahar kafin Dzad ya roki su baba Alhassan din sosai suka nufa Zaadens. Motocin AZIZ da securities dinsa dauke hanya sukai sukam zuwa gida. Maheer ne ya lura da hakan ya sanarwa dad. Dad baba alhassan yayiwa magana sai gashi ya kira AZIZ din yace ya dawo. Sbd kaunar da Baba Alhassan yayiwa Ummitah da kasancewansa mahaifi ga Sayd ya saka baya taba tsallake umarninsa da maganarsa sbd shine wanda ya zama Uba nagari mai kare mutunci da gatan Ummitah a lokacinda baya nan shiyasa matsayinsa a ransa yakeda mahimmanci. Ajiyan zuciya ya sauke tareda dago idanuwansa da sukai wani irin laushi suna bada sexy vibe ya kalli Sayd da ido yai masa alaman su juya. Juya motar sukai securities ma juyowa sukai aka nufi zaadens din. *******Tinda Maheer ya kira ya sanarwa Anny an daura auren wata farin cikin data sake rufeta dakin Jannah din ta nufa ta bude kai tsaye ta shiga fuskanta cikeda farin ciki da murna. Zaune jannah din take bakin gado daga ita sai towel zata shiga wanka sbd ta samu karfin jikinta ya dawo sosai wayarta take kalla tanason kunnawa sbd tasan Ammar yana can yana kiranta coz by now ta riga ta zama matarsa burinsu ya cika dagashi din har ita amma kuma batajin farin ciki na shigarta kaman yanda tai tsammani. Kallanta Anny tayi tana cewa "Jan, Yaya haka? Baki shirya ba haryanzu yau daurin aurenki? Pls yauri kiyi wanka ki fito kina buqatan shiryawa kafin angonki ya iso" Dago idanuwanta tai ta kalli Anny din wanda farin cikinta yake a bayyane Jin tayi inama farin cikin Fuska da zuciyar Anny ya dawo kanta ta nunawa duniya tana cikin tsananin farin cikin wannan ranar da burin Ammar da nata dana Mimi ya cika. Numfashi me sanyi ta sauke ahankali tareda miqewa ta nufi toilet ta shige tana sakawa ranta dole daga lokacinda ta fito toilet din da farin ciki zata fito sbd tabbas ranar farin cikinta ce koba komai zatai farin ciki da rayuwar tattali a hannun Ammar dan haka bai cancanta wannan Yanayin daga gareta ba ya cancanta ya dawo ya taddata cikin Adon farin ciki. Wanka tayi cikin nutsuwa ta fito tana fidda wani irin qamshin daya gauraye dakin me sanyi. Har lokacin Anny na dakin ta fiddo mata kayan sawa na wani black Applique Lace mai Adon dark purple a jikinsa me tsadan da baida hayaniya ko kadan. Dinkin half boubou ne da straight skirt, Zaunawa tayi tafara shirywa fuskanta ba kaman farko ba daidai gwargwado ta sake ta dawo jannah dinta duk da zuciyarta sam ba walwala. Shiryawa tayi batareda makeup ba sai eyeliner kawai da lip gloss kadan shima da baama ganinsa Amma kuma tayi wani nutsatsiyar kyau sbd skin dinta dake glowing sosai sbd gyara da hutun da aka taso cikinsa. Simple English gold sarka da earrings ta saka da zobe daman akwai English gold zoben dayake hannunta koyaushe sai ha qara daya suka zama biyu. Bata iya daura dankwali ba dan haka Anny ce ta tayata daurawan cikin sauki mara hayaniya. Qamshinta kadai sake saka Anny farin ciki yake idan ta tina Daga karshe dai ta zama family da AZIZ LIMBA wanda hakan shine burinta shiyasa take jin kaman tafi kowa farin ciki da wannan auren sbd bata hangowa kanta talauci tafe ba ko kadan jin dadi da hutu kawai. Hannu jannah ta miqa zata dauki wayarta Anny tace "Karki damu ki kunna wayarki anriga an daura auren tin kusan mintina 50 da suka wuce ko awa daya ma Kin tashi daga Jannah Zad kin koma Jannah Limba..." Dago idanuwanta tayi cikin sanyi ta kalli Anny din wadda batasan meta fada ba gurin sauri. Wayarta data kunna ce kira ya shigo wanda kaman ana jiran ta kunna wayar. Sweety Falaq Aziz" shine sunan data gani akan wayar dan haka ta sauke ajiyar zuciya me sanyi tana kokarin dauka Maheer ya shigo dakin yana kallanta cikeda farin cikin ganinta tayi kyau sosai ta fito a amaryanta me cikakken gata. Hannu ya miqa mata yana qarasowa gurinta yace "Congrats my darling, Kin zama mace ayau aure igiya 3 ne akanki, Congrats my baby" Rungumesa tayi idanuwanta na cikowa da hawaye sedai kafin su sauko Saleem shima ya shigo dakin ya ware mata hannu yana cewa "My love ta zama matan aure, Allah ya sakawa aurenki albarka ya baki farin ciki me dorewa, Zakiyi rayuwan kwanciyar hankali da farin ciki sosai a hannun LIMBA yana cikin best mutane dana sani" Gangarowa hawayenta sukai tana qanqamesa shida Maheer lokaci daya sbd har lokacin jin take kunnuwanta na ji mata sunan AZIZ a matsayin wanda suke ambata mijinta kuma kunyar tambaya take sbd kada ya zama tana tambayar wani da auren wani akanta dan haka ta zabi yin shiru tana barwa kunnuwanta abinda suke jiwa kansu. Kamo hannunta Maheer yayi suka fice Saleem kuwa gurin Mimi data qi fitowa ya nufa har lokacin bacci takeyi ya tabata ya duba yaga lafiyanta kalau baccin dai takeyi sai kawai ya kyaleta sbd ya fahimci dole an bata wani maganin ne sbd ta samu nutsuwa daga shock din data shiga jiyan na tension da akace anshiga na faduwan jannah da baya nan. Anny kuwa itama cikin nata adon na alfarma ta fito tabi bayan Saleem zuwa gurin baqi daketa tambayar Mimi tana ce musu batajin dadi sosai an samu ta kwanta tana dan bacci ne. Mommy matar Daddy mahmoud ce ta tsaya akan baqin sunata kaida kawo cikesa farin cikin ana harkan girma da kwanciyar hankali sbd bawai bikin hayaniya bane. Palon Dad Maheer ya nufa da ita Suna kokarin shiga palon hancinta ya shaqo mata kamshin daya sakata dago kanta da idanuwanta ahankali ta kalli kofar gabanta na faduwa. Jin tayi kafafunta na neman sanyi dan haka ta dan dakata tana kallan Maheer. Juyowa yayi ya kalleta duk saiyaji ta basa tausayi me tsanani dan soyayya batai musu adalcin dataiwa Jan dinsu mummunan kamun data koma kalar tausayi sbd ganin kaman wanda take tsananin son baya mata irin wannan son. #MAMUH #BEST LOVE #CRAZYLOVE #BESTREVENGE #BROTHERsLOVE ZAFAFA BIYAR KALBIM 500 mamuhgee A DUNIYATA 500 Huguma AJIYA A DUHU 500 Billyn Abdul KIRJIN ME HANKALI 500 Miss xoxo Pay at 0022419171 AccessBank Maryam sani gummi Shedan biya 09033181070 Or mtn vtu at 09032345899*_KALBIM_* _Mamuhgee_ 59 *TALK WITH SIDDEEQAH* Operation Ciniki Dole 08149588205 Ni Olayyah na shiga uku na kwashe kudi na saro kaya domin in fara kasuwanci online, na gaji da zaman sai Yallaɓai ya bani kudin kashewa, kullum ni ce koma baya cikin danginsu, dukda yana kokarin sa, amma dai gwara in nemi na kaina kodan yan uwa da iyaye. Amma bari in kira Besty nah Huriyyah nasan zata samu maganin wannan damuwar tawa. Tunda na kira Huriyya na faɗa mata abunda ke hanani Bacci ta faɗa mun wani sirri da ya girgizani. Wato ashe itama da ta fara business online kuma bata ciniki amms tunda aka bata number din Coach Saddiqah komai ya fara tafiya daidai a kasuwancin ta ( Talk with Saddeeqah). Tunda ta shiga OPERATION CINIKI DOLE ONLINE BOOTHCAMP komai ya warware mata ciniki babu kama hannun yaro. https://wa.link/8al2f0 Ai ba shiri na nemi Coach Saddiqatu nima domin in shiga tsarinta na Saddeeqah Biz Growth Academy. Kuma Alhamdullilah ina shiga nafara ganin canji a business dina, har ma sabon online business na buɗe daga cikin abunda na koya a Operation Ciniki Dole Online Boothcamp. https://wa.link/8al2f0 Gaskiya wanda ya koya a wurin ƙwararriya ya huta domin ko dubu 100,000 akace in biya in shiga OPERATION CINIKI DOLE ONLINE zan biya domin amfanin da na samu cikin Boothcamp bazan iya faɗaba, gashi yanzu na samu na sayi machine din delivery na maida daki guda shago cikin gida na. Hurayyah ta taimaka da ta haɗa ni da Coach Saddiqah. OPERATION CINIKI DOLE ONLINE ya bani damar yin ciniki yadda ya kamata ba tare da wana damuwa ba. Indai kina business ko kina son ki fara Operation Ciniki Dole Online Boothcamp shine ajin farko da Coach Saddiqah zata rike hannun ki ta nuna miki duk wani sirri da dabaru na kasuwancin online. Daga rashin ciniki zaki koma sold out domin kuwa zaki dinga yin 6 figures monthly, in kin shiga OPERATION CINIKI DOLE ONLINE BOOTHCAMP baki ga sauyi mai kyau a business dinki ba za'a maida miki kudinki bayan 90days. Da Naira Dubu Goma kacal Pre-lunching Price zaki samu damar shiga OCD.( Kina biya zaki fara kwasar ilimi) Zakuma ki iya jira sai 20th January ki biya Naira Dubu Ashirin. ********* Janyota kusa dashi sosai Maheer yayi yana kama hannunta daya ya riqe cikin kulawa da tsananin kaunarsa datake bayyane suka shiga palon.. Kanta a qasa yake amma a hankali ta dan rife idanuwanta sbd qamshinsa daya gauraya palon duk da akwai nasu Maheer da dad harma dana su Alh saad dika masu tsadar ne amma qamshin nasa ya fita daban tana jinsa a cikin numfashin datake shaqa yana isa zuciyarta yana karya dukkanin kuzarinta. Kasa dagowa tayi sbd sanin tabbacin yana palon dan haka Mimi kawai taji tana buqata a wannan lokacin sbd ta rungumeta ta samu nutsuwa daga uwa da karfin gwiwa. Bata qarasa isowa tsakiyar palonba Ammar daya farka cikin wani irin tsananin nauyi da ciwon kai yana saukowa daga gadonsa daqyar ya iya duba time baisan lokacinda jiri na dibansaba ya fito zuciyarsa na neman faso kirjinsa ta fito sbd tsananin harbawan datake ba daidaiba yana jin kaman zai rasa numfashinsa. Dakin Mimi yai niyar nufa ya fasa ganin akwai baki a gidan dan haka kai tsaye ya nufi palon Dad yana isa Jannah da maheer na shigewa da sauri ya qaraso idanuwansa akan Jannah baya ganin komai da kowa sai ita. Maheer ganin yanda Dad ke kallan bayansu ya sakasa juyawa a hankali cikin basarwa ya kalli bayan idanuwansa suka sauka akan Ammar dayake sako kai palon a mummunan yanayi. Sayd dayake kusa da kofar shigowan Kallo daya yayiwa Ammar ya juya ahankali ya kalli uban gidansa wanda yake zaune a kujera hankalinsa kwance yana fidda wani irin kwarji kamewa daga jannah din data shigo har Ammar din dake shigowa ko inda suke bai kallaba duk da babu wanda baisan da zuwansa a gurinba cikinsu sbd ita yasan ta shigowanta a gurin,Ammar dinma kallo daya yayiwa Dzad da Maheer ya faminci Ammar suke kalla a kofa sbd yanda yanayinsu ya nuna. Sayd akwai abinda ko AZIZ bai kallaba bare magana yana gane umarninsa ko abinda yake nufi kokuma abinda ya kamata yayi dan haka miqewa yayi. Gadan gadan Ammar ya nufo Jannah wadda batasan dashiba tana kokarin bude baki ta gaidasu Baba Alhassan.. Kafafunsa da hannuwansa har wani rawa sukeyi ganin manyan rigunan shaddodi masu shegiyar tsada da huluna masu tsadar suma suna daukan ido a jikin kowa Jin yayi ma suna kashe masa ido sbd masifar dayakeji tana kunnuwa a kirjinsa da cikin kansa Jannah din yake kokarin kamowa jikinsa tukuna yayi magana sbd yafisan duk abinda zai fada ko tambaya ya zama tana hannunsa already sbd kada a a rabasa da ita dan ayau yakeson a daura musu auren kaman yanda aka tsara ba dagawa, Ayau yakeson mallakarta,.ayau yakeson maidata cikakkiyar macensa ta yanda babu iya rasashi da ita ko a magana bare a wani aikin. Yanda ya tinkarota kai tsayen zai kamota Sayd yasha gabansa ahankali cikin nutsuwa tareda kallansa da idanuwansa da suke nuna zai iya rabasa da hannuwansa har lahira idan suka sauka akan jannah din. Su baba Alhassan kallan kofar da Ammar din ya shigo sukai cikin mamaki Dad Maheer ya kalla cikin mamaki da tashin hankali alamar yayi handling din Ammar din yayi masa batareda baqin sun gane ba. Ammar cikin tsananin zafin gaske da yawon dayaji kaman tsintsaye nai masa cikin kai ya kalli Sayd zai ciresa daga gabansa ya wuce yace "Kasan me kakeyi? A lokacin Jannah ta juyo da sauri jin Ammar tana ganinsa cikeda mamaki take kallan yanayinsa ta daga kafa zata nufess Sayd ya juyo ya kalleta cikin nutsuwa da bata girmamawa da hannu ya nuna mata hanya yana matsawa gefe da nutsatsiyar sauti yace "Pls Mrs LIMBA" Hanya da inda yake nunawan cikeda girmamawa ta kalla da sauri hannuwanta na dan rawa cikeda mamaki da tsoro sai alokacin ta iya daga ido ta kallesa yana zaune dukansu basu ishesa kallo ba wayarsa ya dauka wadda Falaq ta kirasa cikeda kwanciyar hankali da nutsuwa ya dauka ya dora a kunnesa yana bude bakinsa yace "Yes Falaq Aziz" Abinda Falaq din ta fada kai tsaye a cikin wayar da wani irin farin ciki ya saka sai alokacin ya saukar da fararen idanuwansa akanta itama shi din take kalla tana neman zarewa ga Sayd bakin rai ya hanata wucewa zuwa ga Ammar wanda ya fara wani vibration yana. Maheer ne yayi saurin isa ga Ammar din ya jasa da karfi cikin kyaftawar ido suka fice Ammar din na kwacewa yana son magana Ammar harshensa jin yake kaman ya karye sbd Bugawan da zuciyarsa ke kokarin yi. Sayd cikin fuskewa ya rufe kofan palon yaja ya tsaya koda Ammar din zai dawo dan da alama yana kokarin zarewa ne dan haka yana taba abinda ba nasa ba zarar dashi zaiyi a cikin gidansu ya tafi yabar musu sabon nakasashen Ammar. Tsit palon yayi kowa ya kasa cewa komai sbd yanayin da aka samu din saida Daddy Mahmoud ya fuske ya kalli jannah cikeda kulawa yace "Jannah ki gaida iyayen LIMBA gasunan" Bakinta rawa yakeyi sosai ta budesa batareda ta iya kallansu ta gaidasu tinaninta duk a rikice ta dena gane komai so kawai take ta fita taje gurin Ammar. Amsawa su Baba Alhassan sukai cikeda kulawa suna mata Addua da saka albarka. AZIZ takeson gaidawa shima amma ta kasa sake kallansa dan haka jiki a sanyaye ta juya tabar palon Dad dinta yabita da kallo cikeda tsananin kauna da kulawa. Maheer kuwa koda ya fita da Ammar din daman Anny taga wucewansa da sauri tayo palon saiga Maheer ya taho dashi dan haka batai wata wata ba ta sake sakasa baccin da zai iya masa illa amma bata damuba. Kallanta Maheer yayi zaiyi magana sbd bayason wani abin ya samu Ammar ta dakatar dashi da cewa "Babu abinda zai samesa for his own good nake masa komai sbd kansa bazai iya daukan wannan tashin hankalin dayake saka kansa a ciki ba so yana buqatan hakan dan ya karba lamarin a hankali" Ajiyan zuciya ya sake yana mata kallan kin tabbata Gyada kai tayi tana kama hannunsa suka fice bayan ya gyarawa Ammar din kwanciya da rufa. Suna fitowa dakin Jannah na isowa da sauri tana cewa "Ina Ammar din, Meya samesa? Yaya na gansa haka? Meyake faruwa ne?? Kokarin fadawa dakin take Anny ta riqota tana cewa "Auren AZIZ LIMBA dayake kanki ne yake faruwa, Ki kula sbd yanzu ke din matan wani ce wanin ma AZIZ LIMBA ake magana" Dakatawa jannah tayi tareda juyowa gaba daya tana kallan bakin Anny kafin ta dawo da kallanta kan Maheer tace "Meyake faruwa? Ance an daura auren to waye aka daura dashi ni banganeba, My Ammar kokuwa wani daban?? Riqota Maheer yayi tareda kokarin kwantar mata hankalin dayaga yana neman tashi sbd tsoro da firgici yace "Kwantar da hankalinki my love kinji, Da AZIZ LIMBA aka daura miki aure sbd samarwa da zuciyanki abinda takeso, Bazamu taba iya hanaki abinda zuciyarki takeso ba koma meye" Rawa hannuwanta suka fara a rikice tace "No,no no Ammar nakeson aura, Ammar nakeson aura basai abinda zuciyana ke so ba, LIMBA bai taba sona ba Ammar ne yake sona, Meyasa zaku rabani da Ammar? Ammar can't take ita zai zare,zai haukace zai iya zama komai akan hakan zai iya komai akan hakan.......... Anny ce ta katseta cikesa takaicin zantukan tace "Kinsan shi LIMBAn waye akan haukar da zarewan? Idan hauka Ammar zaiyi to ni banga alamar akwai rashin haukan a tattare da LIMBA dinnanba ki dena ganinsa kaman baya ji ko gani, Kima aje LIMBAn kinga Sayd? Kinsan komai zai iya akan LIMBA? Kina ga bazai iya daukan ran Ammar dinba akan LIMBA" Wani kallo Maheer yayiwa Anny din yana cewa "Ke me kike fada? Stop scaring her, Kina daga mata hankali cant you see tana cikin damuwa da firgici" Janyo jannah din yake kokarin yi tan kwacewa tana son shiga dakin Ammar wanda a daidai lokacin Mimi data taso ta iso gurin jikinta va wani karfi. Da gudu Jannah tayi gurin Mimin ta rungumeta tana fasa wani kuka me sanyi tana cewa "Mimi Ammar bazai iya daukan wannan hukuncin ba, Inason a warware auren dan Allah a dauramun da Ammar" Mimi wasu hawaye ne masu radadi suka gangaro mata dan daman koda ta fito ta fahimci tabbas andaura auren yau Amma bata dauka zasu iya daurawa wani auren jannah ba Ammar ba. Rungume jannah din tayi batareda ta iya cewa komaiba sbd ciwon datake ji yana cike zuciyarta da bacin rai me tsananin gaske. Dakin Ammar Mimin ta ja jannah zuka shige batareda tacewa Anny da maheer komaiba suka rufo kofa. Kallo daya Mimi taiwa Ammar zuciyarta ta karye ta share hawayenta tana zaunawa gefensa. Jannah ma gefensa ta zauna tana ambatar sunansa Mimi ta hanata tabasa da hannuwanta. Kuka jannah din ta fasa wanda ta rasa na menene amma dai tasan tsananin tausayin Ammar bazai taba barintaba har abada da kuma kaunar da suka taso a cikinta ta kusanci da shaquwa. Anny da maheer ma basu samu cewa komaiba sbd ganin Mimi ta daure fuska sosai suka juya suka bar gurin zuciyar Anny fes. Acan palo kuwa Sun fito sun fice sunbar zaadens din zuwa gida wanda Falaq ta matsu daddynta ya dawo sbd yau itace ta tayasa shirin daurin aurensa ta rakasa har mota tana jin kaman ta hanasa zuwa gurin daurin auren ya wuce ya dauko mata Jannah din kawai ya fara kawowa nan. Suna isowa Falaq ta fito da gudu Fiddausi tayi saurin riqeta tana hanata gudun sbd kada matsala ta biyo bayan gudun. Yana fitowa motan da sauri ta qarasa gurinsa ta fada jikinsa tana cewa "BestDaddy ya zama nawa nida Jan" Dariyar zancenta Baba alhassan yayi yana cewa "Wannan baturiya bata da hausa ko kadan sai iyayi da surutu" Sayd ma dariyar zancen nata yake yana cewa "Aa daya a cikinku dai zai daukesa" Sake qanwamesa tayi tana cewa "No,Tin farko har karshe nawa ne ni kadai yanzu ne dai na yadda ya zama namu mu biyu da My jan sai kuma babies biyu da kawai nakeso ta haifo mana sun isa banason na bawa Daddyna da yawa" Kallanta AZIZ din yayi da idanuwansa yana mamakin yanda haryanzu ta kasa wayo duk da girmanta. Sayd tsokanarta zai sake yi AZIZ ya kallesa saiya fasa fadan abinda zai fada yana dariya yace "6 mukeso" Da wani irin tsalle ta kallesa tana dawowa da kallanta kan Daddyn zatai magana ya girgiza mata kai ahankali alaman Ba haka bane kafin ya kalli Sayd din yana cewa "Zaka rikitamun ita ko?" Dariya sosai Sayd ya sake yana shigewa palo yana cewa "Ba ruwana a bakin mama naji, Kuma ashe da gaskiyan mama wata a gidan nan batada wayo sam" Jin sunan Mama ce ta fada hakan kallansa tayi da sauri sbd tasan baya wuce umarnin mama daidai suna shiga palon tace "Daddy d gaske kanne har 6 zaka mun?? Mama dake fitowa dakinta cikin mamaki tace "Ke bakinki komai fada yake ko?? Uban naki kikewa wannan tambayar? Tura baki tayi tana son amsarsa sbd jin tayi kaman ma batason ko guda daya zatai magana magana Mama tayo kanta da gudu tayi bayansa tana cewa "Ni banason ko daya ma na fasa abarni daga ni sai Jan mun isa" Mama sake kallanta tayi zatai magana ya bude baki yana janyota gabansa yace "Babu wanda zai zo ya dameki da daddynki, Amma karki sake maganar nan kwata kwata ok?? Gyada masa kai tai tana dawowa mood dinta na baya tace "Daddy yaushe Jan zata taho? Yau? Anjima? Wat time? #MAMUH ZAFAFA BIYAR KALBIM 500 mamuhgee A DUNIYATA 500 Huguma AJIYA A DUHU 500 Billyn Abdul KIRJIN ME HANKALI 500 Miss xoxo Pay at 0022419171 AccessBank Maryam sani gummi Shedan biya 09033181070 Or mtn vtu at 09032345899*_KALBIM_* _Mamuhgee_ 60 *TALK WITH SIDDEEQAH* Operation Ciniki Dole 08149588205 Ni Olayyah na shiga uku na kwashe kudi na saro kaya domin in fara kasuwanci online, na gaji da zaman sai Yallaɓai ya bani kudin kashewa, kullum ni ce koma baya cikin danginsu, dukda yana kokarin sa, amma dai gwara in nemi na kaina kodan yan uwa da iyaye. Amma bari in kira Besty nah Huriyyah nasan zata samu maganin wannan damuwar tawa. Tunda na kira Huriyya na faɗa mata abunda ke hanani Bacci ta faɗa mun wani sirri da ya girgizani. Wato ashe itama da ta fara business online kuma bata ciniki amms tunda aka bata number din Coach Saddiqah komai ya fara tafiya daidai a kasuwancin ta ( Talk with Saddeeqah). Tunda ta shiga OPERATION CINIKI DOLE ONLINE BOOTHCAMP komai ya warware mata ciniki babu kama hannun yaro. https://wa.link/8al2f0 Ai ba shiri na nemi Coach Saddiqatu nima domin in shiga tsarinta na Saddeeqah Biz Growth Academy. Kuma Alhamdullilah ina shiga nafara ganin canji a business dina, har ma sabon online business na buɗe daga cikin abunda na koya a Operation Ciniki Dole Online Boothcamp. https://wa.link/8al2f0 Gaskiya wanda ya koya a wurin ƙwararriya ya huta domin ko dubu 100,000 akace in biya in shiga OPERATION CINIKI DOLE ONLINE zan biya domin amfanin da na samu cikin Boothcamp bazan iya faɗaba, gashi yanzu na samu na sayi machine din delivery na maida daki guda shago cikin gida na. Hurayyah ta taimaka da ta haɗa ni da Coach Saddiqah. OPERATION CINIKI DOLE ONLINE ya bani damar yin ciniki yadda ya kamata ba tare da wana damuwa ba. Indai kina business ko kina son ki fara Operation Ciniki Dole Online Boothcamp shine ajin farko da Coach Saddiqah zata rike hannun ki ta nuna miki duk wani sirri da dabaru na kasuwancin online. Daga rashin ciniki zaki koma sold out domin kuwa zaki dinga yin 6 figures monthly, in kin shiga OPERATION CINIKI DOLE ONLINE BOOTHCAMP baki ga sauyi mai kyau a business dinki ba za'a maida miki kudinki bayan 90days. Da Naira Dubu Goma kacal Pre-lunching Price zaki samu damar shiga OCD.( Kina biya zaki fara kwasar ilimi) Zakuma ki iya jira sai 20th January ki biya Naira Dubu Ashirin. ************* Kallan fuskanta yayi yana sake ganin doki da murnan dabai saba ganinta dashi ba idan baa kansaba, "Meyasa take tsananin kaunar wadda bai kamata ta kaunata din ba" shine tambayar da zuciyarsa take masa yana kallan Falaq din. Sake riqe hannunsa tai tana cewa "Daddy pls yaushe ne zata taho?" Kaine zakaje ka daukota? Ka aikani na dauko ta yanzu pls BestDaddy" Numfashi ya sauke yana shafa fuskanta yanajin kaunarta na sake ratsasa, Ayau zuciyarsa cikin tsananin qunci da daci take sbd kaddarar auren daya shiga tsakaninsa da familyn da bai hada tsanarsu da komaiba amma ganin farin cikin dayake fuskan Falaq wanda daga zuciyarta yake fitowa saiyaji ya dan samu sassaucin tsananin dacin dayake ransa. Bude baki yayi cikin kulawa da nutsuwa yace "Karkiyita murna da yawa tareda tsalle tsallen nan banason wasa da lafiyanki kin sani so ki kula sosai okay? Gyada kai tayi tana cewa "Zanyi amma daddy pls when zata taho? Bai amsa tambayarba ya wuce palonsa yana jin mama na kiranta. Yana shigewa cire babban rigan jikinsa yayi tareda zame kayan duka sbd ya samu sakewa. Wani wankan ya sake yi ya sauya kaya zuwa qananun kayan D&G bai fitoba ya kashe wayoyinsa dan hutawa. Su mama kuwa bikinsu sukeyi cikeda farin ciki da kwnaciyar hankali sbd su anty maryam duka da iyalan Alh Saad din dana Alh Ahmed duka suka gidan anata taya mama murna. Sayd ma shigewa yayi dan hutawar sbd Uban gidansa na hutawa ba wani aiki. Dayake Fahad ma a mansion din ya sauka shi kam yana cikinsu mama da mutuniyarsa falaq kafin daga baya ya fita zuwa wani guri. ***Karfe 4 da mintina Ammar ya farka yana fara motsawa Mimi da jannah dake dakin har lokacin sukai saurin yi kansa mama na ambatar sunansa tareda kamasa ya tashi zaune ta rungumesa da sauri hawaye na gangaro mata na tsananin kaunarsa me karfi da tausayinsa. Jannah ma hawayen ne suke gangaro mata tana kasa dagowa ta kallesa tana jin tsananin tsanar zuciyarta data kasa riqe amanar shekara da shekaru, Ammar bai cancanci hakan daga gareta ba, Taci Amanarsa taci amanar kanta sbd ta sani har abada wanda aka aura mata din bazai taba sonta kamar Ammar ba wanda zai iya vada rayuwarsa akanta. Kansa da yayi masa tsananin nauyi da zafi ya dan dafe kafin ahankali ya bude idanuwansa da sukai jajir alamar baccin dolen da aka sakasa zuciyarsa bata hutaba ko kadan. Akan jannah ya saukar da idanuwansa ya kafesu akanta yana mata wani irin kallo zuciyarsa na karban wani azababben yanayi me tsananin ciwo da radadi, Tinda Allah ya saka masa tsananin son jannah tin tana cikin mahaifiyarta har isowanta duniya da gwagwarmayar neman lafiyarta zuwa yanzu bai taba kawowa ko a mafarki ko tinanin Jannah zata iya zamowa matar wani ba duk duniya bayansa, Da ransa da lafiyarsa da hankalinsa da tinaninsa aka daura auren jannah da wani yana kwance yana baccin Asara da baqin cikin da aka sakasa sbd cimma buri batareda an dubi nasa halinda zai shiga ba a rashinta.... Rintse idanuwansa yayi sbd wani irin radadin daya yanki zuciyarsa da kirjinsa yana kasa riqe radadin ya rintse idanuwan. Mimi jin saukan hawayensa masu wani irin tsananin zafi taji a bayanta wanda tajisu tamkar sun sauka a zuciyarta ne dan haka bata san lokacinda ta fasa qaramin kuka me sautiba dan tasan babu a duniya abinda zaa fadawa Ammar din akan wannan lamarin ya sassauta radadinsa, Anyi masa illar da har abada bazai warke ba sedai samun sasssauci, Jannah ganin hawayensa zubewa tayi qasa tana fasa kuka itama tana son ambatar sunansa amma baqin cikin kanta datakeji ya hanata fada. Gangarowa hawayensa keyi ahankali akan bayan Mimi datake rungume dashi kafin jikinsa ya fara rawa ahankali yana kakkarwa ta sake qanqamesa da karfi tana girgiza masa kai tana cewa "Ammar no pls, No pls, karka bari ka shiga wani hali zuciyana bazata iya daukaba" Dad ne ya bude kofar dakin ya shigo Maheer na bayansa suna ganin ya farka suka qaraso kowannensu idanuwansu na kansa. Yanayinsa ya saka Maheer saurin isa garesa ya janyosa jikinsa ya qanqame yana kokarin hana jikinsa jijjigan dayake yana jin zuciyarsa na karyewa. Dad ma qarasowa yayi daidai lokacinda Ammar din ya rikice gabaki dayansa komai na jikinsa rawa yake idanuwansa a rintse yana sake qanqame Mimi maheer kuma na sake qanqamesa. Cikin sauri Dad ya kalli saleem daya shigo dakin yace ya kira dr. Da sauri saleem ya ciro wayarsa yana kokarin saka kiran. Daddy mahmoud ma qarasowa yayi dakin cikin damuwa da kulawa yana kallan Ammar din yace Maheer ya cire masa Cardigan din dake jikinsa. Mimi da maheer dinne suka cire masa a lokacinne jikinsa ya sake gaba daya. Maheer cak ya daukesa tareda nufar toilet da sauri Dad ne ya kunna masa ruwan dumi aka zaunar da Ammar din har lokacin maheer na riqe dashi dan haka ruwan su biyu yake jiqawa shima dad din kusan ya jiqe amma dai basason Ammar yana passing out sbd likitarsa data bada umarnin hakan a dena barin yana suma. Cikin ruwan Daddy mahmoud ne da jannah suka shiga ruwan lokaci daya suna girgizasa tareda kiran sunansa cikin tsananin kulawa da son ganin idanuwansa sun bude. Qara gudun ruwan Dad yayi sosai Maheer na sake riqesa da kyau. A cikin qanqanin lokaci gabaki dayansu suke neman zarewa da tashin hankali da firgici sbd Idan aka cire son ran da sukai masa wannan karan to kaf familyn bayan jannah babu wanda ake tsananin so irin Ammar din sbd jinin Zeynab ne da basu hadata a duniyarsu da komaiba, Su kansu a yanzu sun rasa gane wace kaddarar ce takaisu ga wannan lamarin wanda basusan Abinda Allah ya boyeba a cikinsa sai kuma Allah ya kaddara jannah din saita fara auren wani wanda ba Ammar ba. Koda Dr ya iso Ammar din bude idanuwansa daqyar jajir wainda bama ya ganin komai dishi dishi yake gani hakama sama sama kunnuwansa kejin sautin sunansa dasuke ta ihun kira. Akan jannah ya tsayar idanuwansa baya ganinta sosai amma yanajin sautin kukanta da yanda take kiran sunansa. Sake rufewa idanuwansa sukai aka cirosa Maheer ne ya sauya masa kaya bayan kowa ya fice ya kwantar dashi a gadonsa da Jannah ta gyara da sauri hannuwanta na rawa tukuna dr yafara dubasa. Palonsa suka koma suna jiran fitowan likita da Maheer dayake ciki shika suna jin kaman su tattaro likitocin abujan kaf suzo su dubasa. Dr ya dade sosai a ciki kafin komai ya daidaita ya fito yana musu bayanin yanda zaa kula da kiyaye Ammar din kafin ya wuce. Dukkaninsu kaman masu zaman makoki haka suka koma tareda manta hidimar bikin da ake gashi dare ma yayi baqi duka sun watse batareda anma tina da maganar kai amarya ba hakama ta bangaren AZIZ din babu wanda yai maganar zuwa daukan Amaryan. Sallan magrib suka fice yi aka bar Ammar din ya huta sbd yanzu baccin nutsuwa ya samu. Mimi ma sai lokacin ta koma dakinta tayi wanka da ruwan zafi sosai jikinta ya sake tai sallah tukuna aka kawo mata abinci da tea me zafi wanda tea din kawai tasha. Jannah ma bedroom dinta ta koma ta kwabe kayan jikinta tai wanka ta sauya kayan zuwa riga da wando masu fadi sosai da kauri tai sallah ta zauna tana adduar Allah ya kawo musu sassaucin wannan kadaddarorin dasuke afko musu daya bayan daya ya maidasu rayuwarsu ta baya. Kowama bayan dawowa sallah wanka sukai suka sauya kaya zuwa na shan iska basu fitoba sai lokacin ishai suna dawowa sallan angyara dining amma basu wani ci abinci ba kowa yawanci tea da snacks yaci sai Saleem ne ma sai Anny sukaci abinci me nauyi. A lokacin ne Ammar ya tashi Mimi da jannah ne sukai feeding dinsa abincin da bai wani ciba amma dai yasha tea sosai shima. Sallah Mimi ta taimaka masa yayi kafin ta basa magani yasha ta zaunar dashi tana kulawa dashi tana rarrashinsa tareda masa adduoi. Jannah ma sosai take basa kulawan duk da baicewa kowa komaiba kwata kwata yaqi bude baki yayi magana sbd har lokacin bai gama dawowa hayyacinsa ba kawai dai ragewa yanayin nasa tayi. Su Dad ma duka sunzo sun dubasa da rarrashinsa har kusan 10 kowa na dakin kafin kowa ya fice Mimi saida taga ya samu bacci ta bar dakin ta koma dakinta tareda jannah wadda itama duk ta damu. Haka suka kwana cikin yar damuwa sbd ga jannah dinma LIMBA yaqi cewa komai akanta amma tinda ba sauri sukeba suma sai basu masa magana ba dan su basuqi yabar musu ita din anan ba tai zamanta dan haka basuma yi tinanin masa maganaba. Washe gari koda Ammar ya tashi ya dawo hayyacinsa Amma zuciyarsa ke tsananin ciwo da zafi dan haka ko fitowa baiyiba hakama rife kansa yayi a daki bayason kowa ya shigo bayan Mimi da jannah babu wanda yakeson gani. Baa takurasa ba Mimin ce kadai sai jannah din ke shiga. *****acan gidan kuwa Falaq ta damu da zuwan Jannah gidan mama ma da bata samu ganinsa ba tin jiyan sai yau kallansa tayi lokacinda ya fito daga hanyar bangarensa a shirye cikin brown Armanis da wayoyinsa a hannu da ipad sai qaramar jakar laptop dinsa Sayd ya qarasa ya karba yana ficewa dasu zuwa mota tace "AZIZ badai tafiya zakaiba?? Fararen idanuwansa ya saukar yana cewa "Mama barka da safiya" Amsawa tai tana sake jefe masa tambayarta cikeda mamaki Yace "Wani aiki ne me mahimmanci da dole saina isa gurin amma insha Allah kwana biyu ne ba jimawa zaayiba" Sake shiga mamaki mama tai tana cewa "To Jannah dinfa? Tin jiya mukaita jiran maganar daukota da yan kawo amarya amma shiru harsu maryam suka gaji suka tafi Yanzu kana maganar tafiya batareda ankawota ba idan ka tafi waye zai kawota to? Falaq datake fitowa dakinta da sauri sanye da kayan bacci tayo gurinsa jin ana maganar tafiya tace "Daddy tafiya zakai? Nidai to a kawo jan kafin ka tafi" Kallanta yayi itada maman kafin ya bude baki a natse dan bayason maimaita zance yace "Idan na dawo zata taho amma yanzu zata zauna acan saina na dawo ayi maganar komai okay? Bata fuska falaq tayi amma kuma ta gyada kai tana cewa "Okay,Amma Besty karka dade kaji? Shima gyada mata kai yayi yana shafa fuskanta yana cewa "Banda yawo da gudu or tsalle tsalle" Mama ma rasa abin fada tai sbd tasan tinda ya fada dole saiya dawon tinda baa shirya komaiba harna inda Jannah din zata zauna dan haka zata bari ya dawo amma idan ya wuce lokacinda ya kamata da kanta zata ta dauko jannah din sedai ya dawo ya taddata gidan nan. #MAMUH #BESTLOVE #CRAZY LOVE #FAMILY #AZIZ AYOUB LIMBA #JANNAH ZAD #AMMAR ZAD ZAFAFA BIYAR KALBIM 500 mamuhgee A DUNIYATA 500 Huguma AJIYA A DUHU 500 Billyn Abdul KIRJIN ME HANKALI 500 Miss xoxo Pay at 0022419171 AccessBank Maryam sani gummi Shedan biya 09033181070 Or mtn vtu at 09032345899*_KALBIM_* _Mamuhgee_ 61 Har mota Falaq ta rakasa tana jikinsa lafe idanuwanta na son narkewa sbd batason ya dade. Sayd daya bawa latif luggage din AY din set biyu na akwatin LV babba da qarama kallan falaq din yayi yana cewa "Keda kikeda wata bestyn meyene zakiyi kukan bakyason ya tafi" Tura baki tai tana kallan Daddynta tace "Daddy kaga Uncle ko? Zagayota yayi da hannunsa a gefensa datake cikeda tsananin kulawa da kauna yace "Kyalesa zai fuskanci aikin da babu hutu idan bai denaba, Waya ce maka tanada bestyn daya wuce Daddynta?" Dadi taji tana murmushi tace "Karka basa aiki me yawa Daddy amma idan ya sake zance ka basa, Kuma banda Besty bayan daddy Jan da kake cewa ba my besty na bace she is my Jan,my Mummy" Kallanta Sayd yayi yana dariya cikeda kauna da kulawa. Daddyn nata kuwa baice komaiba motan da aka bude masa ya shiga tareda kissing hannunta tukuna ya saki yana sake cewa ta kula. Mota Sayd ya shiga Latif yaja suka bar gidan ta juya ta koma ciki tana tsallen zaadens zata daman jira kawai take ya tafi din taje taga Jan. Tana shigowa gurin mama tai tana kwala mata kira tin a palo. Mama dake daki tana waya tana jiyota taci gaba da wayarta sbd tasan shirme ne kawai ko karar Fiddausi zata kawo. Tana shigowa dakin ta haye kafafun maman tama cewa "Mama dan Allah zani gurin Jan" Mama dake waya aje wayar tayi tana kallanta tace "Ke haryanzu dai Allah bai kawo miki nutsuwa da sanin kin girma ba ko fatima? Yanzu ki dubi girmanki kizo ki haye kafafuna ko tausayin tsufana bakyaji ko? Sake gyara zamanta yayi akai duk tama kere maman daga zaunen tana sake bayyanarda shagwabanta tace "Mama ai kece kika koyamun hawa kafafunki ko bayan na girma ai kina dorani idan zaki rarrasheni to yanzu ma ki rarrasheni Daddyna ya tafi ya barni" Hannu mama ta daga zata zuba mata duka a baya tai saurin tashi tana cewa "Me zakiyi mama? Dukarwa the great AZIZ AY LIMBA 'ya? Dan Allah mama wai yaushe zaki dena dukana ne, Nafa fara zama yan mata" Ajiye wayar hannunta mama tai gefenta tana cewa "Sai ranar da kikai hankalin fara zama yan matan tukun zan dena" Dawowa tai ta zauna gefen maman tana cewa "mama pls zanje na dubo my Jan kinji" Itama kanta maman ya kamata ta dubota tinda dai yayi tafiyarsa baice komaiba dan haka dole taje tayi gyaran zance dan idan aka biyesa haka zai bari auren ya gantale dan haka ta kalli falaq din tace "Bari zuwa anjima zamu tafi tare nima zanje godiyar 'ya da suka bamu aure sbd jibi idan Alh Alhassan idan zaije gaisuwa wata rasuwa gida tare zamuje nima zan dubo dangi shekaru da yawa" Cikin mamaki tace "Mama nidai to bazanje ba gurin jan zan koma saikin dawo" Ko kallanta mama bataiba tace "Jan din daya kamata mu dauko bamu daukonba sai kuma kije ki zauna mata?" "Eh nidai mama gurinta zan zauna gaskia kafin ki dawo, Ga Fiddausi nan zata tayani zaman can din bazan dameta da komaiba tinda Daddy bayanan nidai ki bari dan Allah naje can din pls mama" Magiya taci gaba dayi amma maman bata tankata ba saima anty maryam data daga wayarta ta kira akan atampopi masu kyau da tsada datake son a kawo mata taje dasu ganin gidan ta rabawa mutane. Falaq kuwa barin palon tayi ta nufi dakinta ta dauki wayarta ta kira jannah wadda wayarta take kashe har lokacin. Wurgi tai da wayarta tana jin ba dadin rashin samun jannah din. Da yamma driver ya daukesu ya kaisu zaadens wanda suna isa cikeda girmamawa da kulawa aka tarbesu har ita Mimin bata nuna komaiba sbd bata iya wulaqanta mutane ba hakama ta riga ta samu kusanci da mama da bazata iya iya nuna mata tsanar dataiwa auren 'yarta da 'danta ba, Dayan babban dalilin kuma shine duk tsanani Zaadens basa barin wani yasan matsalar data shafi iya sirrinsu na familyn dan haka bazata taba barin mama tasan ansamu cin amana a cikin ahalin nasuba na cutar Ammar da akai. Da farin ciki ta tarbeta tana jan Falaq a jikinta datake cikeda murna tana cewa ina jan dinta. Gaisawa kawai tai da Mimin tabar palon Fiddausi na biye da ita ta nufi dakin jan tana kwala sunanta da My Jan. Jin muryan Falaq a gidan ya saka jannah dake kwance tashi tana daidaita yanayinta cikin nutsuwa ta sauko gadonta tana nufar kofa daidai suna shigowa Falaq ta fada jikinta tana cewa "My Jan wayanki a kashe duk na damu sbd tin jiya naketa jiran zuwanki shiru" Cikin kulawa da kauka fuskanta a sake sosai tace "Duk ki aje wannan nima nai missing Baby falaq Aziz" Dariya falaq din tai suna qarasowa ciki suka zauna Fiddausi na gaidata cikin girmamawa da sakewa itama tace "Tin kiya kam munata jiranki Mutuniyar ma daqyar tai bacci" Dariya falaq tai tana cewa "Na dena damuwa sbd Daddy yana dawowa zata koma can shikenan" Labarin yanda sukai bikinsu acan LIMBAs tafara bata tana nuna mata hotina harda na daurin aure data saka fahad ya tura mata duka. Akan fuskan AZIZ dayake zaune sanye da manyan kaya a lokacinda ake daura auren masu hoto suka ringa daukansa ta xubawa idanuwanta tana kalla. Ganin yanda take kallan hoton jikinta na mutuwa tausayin kanta na rufeta na gangancin dataiwa kanta na barin son datake wa wannna bawan Allahn ya fito fili gashinan ta qare da aurensa bayan bata ga alamar zata taba daraja a hannunsa ba, Falaq ta sauya hoton da nemo wani hoton dayafi fitowa sosai yayi wani irin kyau a cikin kayan daurin auren nasa duk da black ne ya saka amma hakan yayi masa kyanda zaka dauka auren farin ciki ne. Numfashi me sanyi a boye jannah ta sauke tana dauke idanuwanta akai tana jan hannun falaq din da akaiwa lalle simpe me kyau da Anty maryam ta kawo me lalle tai mata tace "Falaq da henna" Kallan hannun tai tana cewa "My first time and i like it" Saleem ne ya shigo dakin falaq ta gaidasa a sake sbd shima yana tsananin kaunarta dan haka mutuminta ne a familyn shi da Anny amma sam bata yin Ammar ko kadan. Fira sukeyi sosai har seda Dad ya dawo gida suka fito suka gaidasa Yana nunawa falaq din kulawa da kauna sosai Mama ma sun gaisa tai godia tareda sakawa auren albarka ta kuka basu hakurin tafiyar gaggawa ce ta kamasa yana dawowa zaa aiko daukan Jannah insha Allah. Shiru dukkaninsu sukai sbd jin lamarin wani iri shi kuwa dad din cewa kawai yayi Allah yakaimu sbd daman baba alhassan ya kirasa ya sanar dashi hakan tareda basu hakuri shida Daddy mahmoud. Lamarin ya mugun sosa ransu sbd kamarsu ace an aure Macen datafi kowace mace daraja da matsayi a familyn kaf ace anbarsu da ita gabansu tsabar wulaqantawa ko kiransu bai samu yi ba bare ita jannah din wadda sai yanxu suke ganin ma kamar baigama noticing nataba. Mimi nauyi kirjinta ya qara akan abinda akaiwa Ammar amma daurewa tai ta nuna itama ai ba komai tinda duk harkan gida ce. Anan suka qara kaiwa dare kafin suka koma gida bayan jannah ta daure cikin jin nauyin maman tace dan Allah abar mata falaq kafin maman ta dawo, Maman tana kaunar jannah amma batai saurin yadda ba saida Mimi ta saka baki dan haka ta amince sbd daman batason zuwa da falaq din kauye dan bazata iya ko kwana daya acan ba kila hakama tana zuwa ita falaq zata san ba AZIZ ne mahaifinta ba Sayd ne dan haka tafi samun nutsuwar barinta anan tinda dai yanxu Jannah kaman Mum dintace. Farin ciki agun falaq baa magana dan haka washe gari koda su mama ke shirin tafiya tini itama Fiddausi ta shirya mata nata kayan a tsadaddiyar luggage dan haka ko daddynta bata fadawa ba da sukai waya. Washe gari tin karfe goma na safe driver ya iso daga zaadens daukanta ta fito itada Fiddausi suka wuce bayan sunwa su mama fatan sauka lafiya. Suna wucewa da mintina suma su maman suka fito da sabuwar me aikinsu da baba alhassan Latif ya kama hanya dasu a cikin wata lafiyayyar tsadaddiyar beymach. Su falaq koda suka isa zaadens a lokacin Ammar da Mimi suka fito a shirye zasu nufi airport suma tafiyar sati biyu zasuyi daga shi sai Mimi sbd ya warware ya dawo mata Ammar dinta su dawo dan tai masa alkawarin dawo masa da jannah hannunsa dan hakan ne ma ya samu ya nutsu zasuyi tafiyar sbd ya dawa a Ammar dinsa ya dawo da jannah hannunsa kota halin yaya koda hakan na nufin kowama ya mutu. Jannah tashiga damuwar tafiyar tasu mimi amma zuwan falaq ya sakata jin ta dawo daidai dan haka suka koma ciki cikeda farin ciki. Da daddare ta gaji sosai da surutu da yawo cikin gidan Fiddausi ce ta kawo musu abincinsu a daki sukaci sukai wanka kowannensu ya shirya cikin kayan bacci. A gefen jannah dake kan sofa zaune tana video call da Mimi falaq ta zauna tana kwantar da kanta kan cinyarta tana kallan Mimi datake nunawa jannah kauna. A karo na farko dataji wani iri akan rashin uwa, Kwata kwata batajin damuwa ko kewa ta uwa sbd mahaifinta ya cike mata wannan gurbin bai taba barinta shiga damuwa ta rashin uwaba, Dashi da uncle da mama da Fiddausi sun tabbatarda bata samu damuwar rashin uwa ba ko kadan. Kewan Daddynta taji ya ciketa dan haka ipad dinta ta tashi ta dauko ta dawo ta sake kwantawa jikin jannah din wadda ta gama wayarta ta ajiye gefe tana kama gashinta na qananun kitson dayake kanta na kusan 3 cuku tanason daurewa dan suna damunta sosai sbd tsayin gashin. Muryansa kwatsam taji a kunnenta cikin wani irin lafiyayyan sauti na mai aji da burgewa yace "Hey Besty" Kallan inda muryan ta fito ta kalla tana sake kitsanta data kama suna dawowa zube. A cikin idon juna idanuwansu suka sauka batareda sanin tana tareda jannah ba hakama itama bata dauka da gasken muryansa tajiba. janye nasa idon yayi batareda ya nuna alamar yama ga mutum a tareda falaq din ba yace "Kina ina?? Daga ipad din tayi kai tsaye batareda tsammaninsu duka ba ta karawa Jannah wadda rigar baccinta mara hannu tana cewa "Ina gurin My Jan,ni banbi inna inda zata tafiba gurin jan nakeso shine na taho tareda Fiddausi" Janyewa jannah tayi daga jikin Falaq din tana barin gurin gabaki daya zuciyarta na dan rawa, Shikuwa kashe kiran yayi gabaki daya yana jefar da ipad dinsa gefen gadonsa dayake sanye da fararen kayan bacci masu santsi da tsadan gaske yana jin bacin ran zuwan falaq zaadens zama harda kwana. #MAMUH# KUYI HKR DA POSTING DA NAKE LATTI UXURI NE AMMA INSHA ALLAH DAGA YAU NA GAMA ZAMU KOMA KAMAN YANDA MUKE DA WURI#*_KALBIM_* _Mamuhgee_ 62 *UMMU_MAHNOOR LUXURIES* (Best luxuries shop) 08034469681 08135142610 Aslm Alaikm ina kuke masu neman luxuries na kayan alfarmar kece raini? Ina masu son su saka sitirar alfarma ta zamani ta manyan mata masu aji da zaa kalleki kallo daya asan sitirar alfarma e kika saka? Shin kunsan me ake nufi sa kayan asalin yan gayu da nuna gayu? Sitirar Alfarma kikeson sakawa? Sitirar da kike ganin manyan mata da ita? Sitirarda zakiyi gayun sallah dake da yaranki a dauka waje kikaje da kanki kika siyota? To kizo ga damarki ta sameki sbd UMMU_MAHNOOR LUXURIES ta kawo miki sauki har gida, Karkice se masu kudi ke iya siya har kema me yar dama zaki samu naki da saukin kudi kuma best quality da kalar zamani data yan gayu, Nidai Mamuh nace duk wadda ke son a buga gayun sallan bana da ita da 'yayanta to tazo gurin UMMU_MAHNOOR LUXURIES tai siyayyar sallanta harma zuwa gaba dan nasan zakuji dadi da fahimtar abinda nake fada akan kayanta💯💯 Abubuwan da zaki samu a gurinta with the best quality na wayayyun mata masu aji yan gayu sune; Atampopi Laces Shadda Materials Shoes Bags Veils Trolleys Jewellerys Oil perfumes Numbers 08034469681 08135142610 Handles Instagram @ummu_mahnoor_luxuries TikTok username @ummu_mahnoor_luxuries Facebook ummu_mahnoor_luxuries ***************** Kallan ipad din hannunta falaq tai tana cewa "Daddy hang up" Tayi mamaki sbd bai taba hakanba yawanci ma shine yake cewa sai tayi bacci ya kashe. Kallan Jannah data isa gado ta haye ta kwanta tana rufe jikinta yayi tayi tana cewa "Jan baki gaisa da daddy ba harya kashe wayan meyasa kika tashi? Kallanta jannah tayi da idanuwanta tana kasa cewa komai kafin ta dan bude bakin tace "Zo ki kwanta sbd kinsan gobe Monday akwai school" Tahowa tayi tana hawowa gadon ta shige abin rufar itama tana cewa "Jan banason school sam" Murmushi me sauti Jannah tai tana cewa "Did your Daddy know that?? "No" tace tana karanta adduarta ta bacci tana rufe idanuwanta. Babu bata lokaci bacci ya dauke falaq din hankali kwance. Ajiyar zuciya Jannah ta sauke ahankali tareda tashi zaune tana zubawa fuskan falaq idanuwanta dake cikeda azabtacciyar soyayyar da batada amfani gareta, Tamkar copy dinsa ne akan fuskan falaq har mamakin kamanninsu takeyi, A duk lokacinda take kallan fuskan Falaq shi zuciyarta take gani, Sake sauke numfashi tai tareda miqa hannuwanta ta gyarawa falaq din rufa tana gyara mata hulan baccin daya zame daga kanta ta sake mata addua tana jin kaman zuciyarta zata bude sbd tsananin kaunar datakewa Falaq din da mahaifinta, Ayau da zata fara kwana guri daya da falaq jin tai kaman baccin ya qaurace daga idanuwanta so take kawai taita kallanta har ta cika zuciyarta. Zamewa tai ta kwanta ahankali tana facing Fuskan falaq din wadda take bacci hankali kwance, Kallanta take a natse tana jin nutsuwarta na dawowa da jin farin ciki na mamaye zuciyarta ahankali Ahaka bacci me dadi da nutsuwa ya dauketa. Da Asuba wayar falaq dinne ta tadasu bacci. Cikin bacci jannah taji ringing din wayar a cikin kunnenta sbd tana ta gefenta akan bedside dan haka hannu kawai ta miqa tana jin bacci na sake cike idanuwanta. Dauko wayar tayi batareda ta duba sunan me kiranba tai rejecting ta ajiye tana dake qaramar tsoki sbd tama manta kwata kwata da ba ita kadaice ba ayau din so ta dauka tata wayarce. Sake kira akai kai tsaye sbd a nasa bangaren tinda yarinyarsa ta fara wayo yake koya mata sallah akan lokaci shiyasa ya sabar mata duk asubar duniya yana nan ko baya nan saiya tadata sallah akan lokaci, tin bata saba ba harta saba yana kira take tashi tayi sallanta a lokaci ta koma ta kwanta, Ayau karo na farko na rayuwarsa da akai rejecting call nasa kuma daga wayar 'yarsa shiyasa kai tsaye ya sake saka kiran. Wannan karan kiran na sake shigowa Jannah ta sake motsawa tana miqa hannu a fusace ta dauka ta batareda ta duba sunanba dan ko gani batayi sosai sbd baccin dayake idonta ta saka handsfree kafin tai magana muryansa ce mai kauri da sautinta yake bada wani irin sexy vibe din da zai iya juyar da kan da yawa wasu idan suka ji sbd a lokutan da ake tashi bacci a lokacin muryan mutane da dama sautinta komawa yake na tada hankalin wasu, So tasa muryan a koda yaushe hakan take idan har ya tashi bacci yayi magana to zai iya daga hankalin me sauraronsa dan haka ahankali muryansa ta bayyana a cikin wayar a natse yana cewa "Why did you reject the call??? Bude idanuwanta dake rufe jannah tai tana kallan sunan dayake kan wayar jikinta na wani irin mutuwa ta tashi zaune tana kokarin hana sautin numfashinta shiga wayar amma saida ya shiga cikin wayar ahankali ya sauka a cikin kunnensa. Cire wayar yayi daga kunnensa yana saka handsfree ya ajiye gefensa yana sake jefa tambayarsa "Why did you reject the call? Yasan ba yarsa bace sbd har abada Falaq bazata taba rejecting kiran Daddyntaba. "Numfashi me dumi ta sake sauke ahankali bugun zuciyarta na dan qaruwa ta bude baki Ahankali da muryanta dake cikin sauran yanayin bacci tace "Sorry na manta na dauka wayana ne" Takaici da mamaki ne ya kamasa lokaci daya kamar bazai tankata ba sai kuma yace "Tarbiyan yarinyana dana gidanku ba daya bane, Tana tashi sallah in time bata taba tsallakewa ba sai ayau karan farko data kwana a inda bai kamataba, Ke baa koya miki sallah kan lokaci bane? This is unbelievable" ya fada yana kashe wayarsa cikeda damuwan abinda yasaka Falaq zuwa zaadens da bai yadda da komai nasuba. Shiru jannah tai da wayar a hannunta tana kalla idanuwanta suka ciko da hawaye masu dumi amma bata bari suka saukoba ta sunkuyar da kanta zuciyarta na daci sbd tinda take a duniya bata san komaiba bayan gata sai ciwon da Allah ya jarabceta dashi, Bata taba sanin ya daci da ciwon fada,zagi ko baqar magana yakeba a rayuwanta, Ta samu tarbiya duk gatanta iyayenta sun tsaya sun bata tarbiya daidai gwargwado hakama itama ta taso da sallah din akan lokaci bisa koyarwan iyayenta da yan uwanta musamman Ammar bai taba tashi sallah da asuba bai kirata ba ta tashi sunyi kusan lokaci daya. Kalamansa ne suke mata radadi amma batasan ma metake ji ba akansu, Ya kirata mara tarbiya ne ita kadai kokuwa harda Familynta?? Falaq ce ta fara motsawa alaman zata farka sbd indai lokacin sallan yayi sbd sabo to sai Allah ya bata ikon tashi. Kallan falaq din tai kafin ta ajiye wayar hannunta ahankali jikinta a sanyaye hawayen idanuwanta n gangarowa ahankali ta zira kafafunta qasa ta sauko tana miqewa ta nufi toiletta shige. Tana fitowa wayart na nuna haske alaman shigowan kira. Falaq ce data tashi zaune idanuwanta suka fara sauka akan wayar taga qatuwar heart ce kawai da kiss take tasan Ammar ne ta sauko gadon tana tura baki tana magana qasa qasa harda buga qafa ta fada toilet. Jannah kuwa mamaki ne ya kamata sosai na ganin kiran sbd ta dauka bazai dake kirantaba tadata sallah. Jikinta dayake mace ta zaunar bakin gado tana daukar wayar ta dora a kunnenta cikin sanyi ta furta sunansa. Ajiyan zuciya ya sauke da numfashin daya kusa barin kirjinsa sbd harga Allah bazai iya rayuwa babu jannah ba, Bazai taba iya moruwa ba idan babu jannah a rayuwarsa, Bazai iya barwa kowa jannah ba, Yana mata wani irin mayen so da bazai taba jin zafi ko ganin laifintaba dan hakanne ma zuciyarsa ta kasa hanasa cigaba da sonta da nemanta tinda auren ance na wata uku ne ya yadda zai jira indai zata dawo garesa ya yadda ya zama wawa mahaukaci mara zuciya ya jirata. Sake ambatar sunansa tai a natse tana danne damuwar datake ranta. Cikin nutsuwa shima ya bude baki yace "Time na sallah yayi" "Na tashi already" Shiru sukai kafin tace "Thank you" Kashe wayar tayi bayan ta fada hakan ta ajiye tana miqewa ta saka kayan sallah sukai sallan tareda Falaq daketa jin haushin kiran Ammar din. Suna gamawa sun dan jima suna Adhzkhar kafin suka koma suka kwanta sbd dukkaninsu yayan hutu ne da basusan wahalarda kai da tashi da wuri ba. Fiddausi kuwa a dakin data kwana gari na wayewa ta fito ta nufi kitchen ta gaisa da masu aikin gidan da chiefs dinsu suna yar fira tana aikin breakfast din falaq dana zuwa school dinta duk da tana SS1 sbd yanayin karatun can dana nan daba irin tsarin wanda tayoba bane sai aka sakata a ss1 sbd tagane na nan din yanda ya kamata amma tana zuwa da abinci sbd yanayin hygiene na abincin school da hankalinsa bai kwanta duka dashiba duk da tsadar school din da abincinsu da kamanma a makarantar qasashen wajen duk da haka na nata take zuwa. Fiddausi na gama hada komai ta jera a tray ta nufi dakin Jannah. Tana isowa knocking tai so daya kafin ta bude dakin ta shiga ta maida ta rufe ta nufi table ta ajiye kayan hannunta tukunta ta zagaya bangaren Falaq ta durqusa bakin gadon tana kama hannun falaq din tareda ambatar sunanta a natse sbd baa tadata bacci cikin tashin hankali koyaushe kaman zaa sakata wani baccin ake tadata. Sake ambatar sunanta Fiddausi tai tana gyara mata rufa. Motsin gyaran rufar ya sakata motsawa Fiddausi ta sake kiran sunanta. Bude idanuwanta tai ahankali tana kallan Fiddausi tace "Banson school bazaki bari na hutaba kafin Mama da Daddy su dawo" Murmushi Fiddausi tayi tana yaye mata abin rufa tana cewa "Ki bari kije yau tukuna sai muyi wannan shawaran daga baya" Bata fuska tai tana miqewa zaune tareda saukowa gadon tana cewa "Fada kawai kikai bazaki yaddaba na sani" Toilet ta nufa Fiddausi tabi bayanta da towel ta kai mata daman already tin jiya aka jere mata kayan wankanta da dauran amfaninta a cikin toilet din duk da koina tsadaddun kayan amfanin jannah dinne masu kyau da tsada amma dai haka itama aka jera nata. Brush da wanka tai ta fito daure da towel lokacin jannah ta farka ta sallami Fiddausi dan haka itace ta tayata shiryawa tai breakfast suka fito. Itace takaita school tareda Fiddausi da baa barin falaq zuwa ko gate ba tareda itaba. Suna zuwa kafin ta shige saida tai waya da Daddynta kafin ta bawa Fiddausi wayanta ta shige suka juya. Suna dawowa gida jannah bacci ta koma sbd duka mutan gidan babu wanda ya tashi. Fiddausi ma komawa masaukinta tai sbd ta gama aikinta na dole waton kulawa da Falaq. Sai guraren 10 suka fito daya bayan daya suna haduwa a dining. Cikeda kulawa da kauna dad ya kalli jannah data zauna kusa dashi tana kama hannunsa tai masa ina kwana yace "Ina Falaq Aziz? "Tana school" Maheer ne ya kalleta yace "Waye yakaita? "Nice na kaita" Shiru sukai dukkaninsu cikeda tausayinta da kaunarta. Breakfast suka fara ci Maheer na cewa "Gobe xan sanar da driver na yaxo tinda safe ya kaita sbd sanyi zai shigeki idan kina wannan fitan na tinda safe" Dagowa tai ta kallesa zatai magana sai kuma ta fasa. Suna gamawa ta koma dakinta tana wayoyinta da chats har kusan 1 da wasu mintina ta tashi tai sallah. Fiddausi dataga lokacin dauko Falaq din yayi ta samu jannah din ta sanar mata. Fitowa tai zuwa daukota Maheer yace ta koma ya aika driver yaje daukota batareda anje da Fiddausi ba. Ko kafin driver yaje school din saida Maheer ya aikesa office ya karbo masa wasu takardun ya dawo gida ya basa tukuna ya koma daukota. Zuwa lokacinda ya isa an dade da tashi daga school din falaq da tinda take a rayuwarta bata taba fitowa daga class ba tareda driver da Fiddausi na gate suka jirantaba sai ayau kuwa, Galabaita da tsoro ne sosai suka shigeta wanda ya saka idanuwanta fadawa sosai sbd sai 3 zuwa 4 aka daukota. Koda aka iso gida da ita duk ta fita hayyacinta daman Fiddausi tinda lokacin daukota yayi taga baa kawotaba bata dake zamaba taketa yawon xuwa gate hankalinta a tashe zuciyarta na tsinkewa gashi tana tsoron kiran sayd ta fada batasan hukuncin da mai gidan zai dauka ba akan hakan. #MAMUH ZAFAFA BIYAR KALBIM 500 mamuhgee A DUNIYATA 500 Huguma AJIYA A DUHU 500 Billyn Abdul KIRJIN ME HANKALI 500 Miss xoxo Pay at 0022419171 AccessBank Maryam sani gummi Shedan biya 09033181070 Or mtn vtu at 09032345899*_KALBIM_* _Mamuhgee_ 63 *UMMU_MAHNOOR LUXURIES* (Best luxuries shop) 08034469681 08135142610 Aslm Alaikm ina kuke masu neman luxuries na kayan alfarmar kece raini? Ina masu son su saka sitirar alfarma ta zamani ta manyan mata masu aji da zaa kalleki kallo daya asan sitirar alfarma e kika saka? Shin kunsan me ake nufi sa kayan asalin yan gayu da nuna gayu? Sitirar Alfarma kikeson sakawa? Sitirar da kike ganin manyan mata da ita? Sitirarda zakiyi gayun sallah dake da yaranki a dauka waje kikaje da kanki kika siyota? To kizo ga damarki ta sameki sbd UMMU_MAHNOOR LUXURIES ta kawo miki sauki har gida, Karkice se masu kudi ke iya siya har kema me yar dama zaki samu naki da saukin kudi kuma best quality da kalar zamani data yan gayu, Nidai Mamuh nace duk wadda ke son a buga gayun sallan bana da ita da 'yayanta to tazo gurin UMMU_MAHNOOR LUXURIES tai siyayyar sallanta harma zuwa gaba dan nasan zakuji dadi da fahimtar abinda nake fada akan kayanta💯💯 Abubuwan da zaki samu a gurinta with the best quality na wayayyun mata masu aji yan gayu sune; Atampopi Laces Shadda Materials Shoes Bags Veils Trolleys Jewellerys Oil perfumes Numbers 08034469681 08135142610 Handles Instagram @ummu_mahnoor_luxuries TikTok username @ummu_mahnoor_luxuries Facebook ummu_mahnoor_luxuries ***************** Fiddausi na ganin shigowar motar harabar gidan ta fito da sauri tana nufar motar hannuwanta har rawa sukeyi ta bude motar. Ko tsayuwa falaq din bata iya yi sosai sbd gabalaita ga ruwa tanason tasha dan haka da sauri Fiddausi hankali tashe tai ciki da ita a lokacin jannah itama ta fito cikin damuwa da key dinta a hannu zataje da kanta ta dubo sbd tin dazun takeson zuwa ana hanata. Ganin Fiddausi da falaq din wadda idanuwanta sukai ciki sosai ya sakata qarasowa gurinsu da sauri tana kamo falaq din jikinta zatai magana falaq ta fasa kuka mara sauti tana cewa "A kira mata daddynta" Fiddausi na jin hakan ta sake shiga tashin hankali tanajin itama gidan takeson bari su koma gida. Jannah da Anny kuwa cikin tsananin kulawa suka nufi dining da ita suka zaunar Fiddausi na zuba mata brown spaghetti da aka dafa dasu carrots da Naman kaza ba tareda qashi ba taje ta kawo mata ruwa masu dumi jannah ta karba tana bata da kanta tana shafa bayanta tana cewa "Am so sorry Falaq ban dauka zaa kai wannan time din baa daukoki ba" Ruwan falaq tasha kafin ta fara cin abincin da Fiddausi ke tsananin son ganin tashi. Taci abincin sosai kafin ta miqe suka nufi daki ta cire uniform tai wanka tai sallolin dake kanta wanda koda ta gamasu sosai zazzabi ya rufeta. Cikin tsananin damuwa jannah ta kira Anny ta dubata ta bata magani baccin wahala ya dauketa. Fiddausi gaba daya jikinta sanyi yayi gashi mama tanata kira tanason magana da Falaq din amma sai karya take mata akan sun fita da Jannah. Daddynta ma so uku yana kira Jannah bata iya daukaba sedai Fiddausi ce take dauka ta sanar dashi bacci takeyi. Na biyu daya sake kira cewa tai tana toilet Na ukun tana ganin kiran zuciyarta ta ringa tsalle da fargaba. Har dare suna jinyarta da tarairayanta tayi sallah ta sake cin abinci a lokacin ta dauki wayarta ta kira Daddynta da kanta Yana dauka hawaye ne na tsananin kewansa da mama suka gangaro mata da muryan da karamin kuka ke zuwar mata tace "I am missing you Daddy pls ka dawo" Shiru yayi yana karantar yanayin muryanta tsawon seconds kafin ya bude baki a natse yace "Meya sameki? Shiru tai tana share hawayenta kafin tace "Ba komai i just miss you Besty" Sayd dayake gabansa ya kalla take sayd ya fidda wayarsa ya saka kiran Fiddausi. Fiddausi na dakinta kiran Sayd y shigo wayar. Numfashi ta sauke ahankali tareda daukan wayar tana fara gaidasa cikeda girmamawa. Amsawa yayi yana cewa "Me yake damun Falaq Aziz? Akwai abinda yake faruwa ne? Sun mata riqon da baya iya musu karya hardai akan Falaq dan haka a natse ta sanar dashi abinda ya faru. Dayake handsfree take komai akan kunnen AZIZ ya sauka kuma har lokacin bai aje wayan dayake da Falaq dinba dan haka numfashi ya sauke batareda yace komaiba. Rarrashin falaq din yayi ya nuna mata zai dawo ta samu tai bacci ya wayar na aiki. Wayar ya kashe Sayd na kallansa yai tinanin zaadens din zai kira sai yaga bai kirasu ba. A zuciyarsa yaso kiran Dzad ya sanar dashi kaf zadeens babu me amfani amma kuma saiya fasa sbd 'yarsa suka taba,sanyin idaniyarsa da zuciyarsa dan haka zasuji yanda yaji. Karfe 4 da mintina kiransa ya shigo wayar Falaq wadda take bacci sosai sbd rashin karfin jikin data kwana dashi. Jannah ce kiran ya tada wadda ta dade batai bacci ba tana kulawa da falaq din. Kaman bazata dauka ba saita tina maganar daya caba mata jiyan akan rejecting kiran dan haka ta tashi zaune ahankali ta miqa hannu ta dauki kiran tareda dora akan kunnenta da sanyin murya tace "Asslm Alaikm" A zuciyarsa ya karba sallaman yana bude nasa bakin yana hadiyewa bacin ran daya kwana a cikinsa yace "Akwai mutum daya a Zadeens dayakeda tinanin daya kamata? Wane irin tinani ne kuke dashi daya banbanta dana sauran mutane? Kunsan bazaku iya kulawa da falaq ba kika saka mama ta bar miki ita? Are you guys for real? Kunsan waye falaq Aziz kuwa? Tafi duka Zaadens da abinda suka mallaka idan kanku bai baku ku kula da ita sbd mahaifinta ba ai zaku kula da ita sbd nacin kaunarta akanki, Kasheta kukai niyan yi kome? Bakwajin komai a gurin kisan mutum ne or wat? Hawayen dake ta tsiyayowa jannah suka ta fara fidda sautin sheshekan kuka ahankali can qasa wanda ya sakasa sakin qaramin tsoki yana kashe wayar yana jin sabon takaici da bacin rai na rufesa. Ita kuwa gudu hawayenta suka qara sosai tana jin kirjinta na nauyi da maganganunsa da suke kai tsaye zagi da qarshen wulaqantawa gashi ko magana bata samun yi yake kashe wayarsa koyaushe. Ajiye wayar tayi tana rufe fuskanta da tafukan hannunta biyu tana girgiza kai alaman bazata iyaba, Bazata iya da aurensa ba, Bazata iya daukan wannan baqin cikin da qarshen wulaqancinba har karshen rayuwarta, Tana tsananin sonsa da kaunar 'yarsa amma bazata iya rayuwa dasu ba ta hakura dan Allah a raba auren nan. Sallah ta sauko gadon taje tayo alwala tayi ta jima tana rokon Allah zabin Alkhairi a cikinsu, Idan Ammar ne Alkhairi a gareta Allah yayi gaggawar kawo mata mutuwar wannan auren da batama san ya sunansa ba. Tana gama adduarta gurin falaq ta nufa ta tadata cikin kulawa tai sallah ta koma ta kwanta bayan ta bata warm milk tasha sbd ba maganar zuwa school yau. Bayan falaq ta tashi guraren 10 tai wanka a daki aka kawo mata breakfast dinta taci wanda jannah din ce take aikin. Wuni tai tana kulawa da ita duk da falaq din ta warwarewanta daman yar wahala ce da bata saba da itaba ta tabata dan haka ta sakewanta sosai. Washe gari tinda safe Jannah ta tashi ta nufi kitchen da ita Fiddausi ta hada mata breakfast da komai na zuwa school sbd ko ayau da asuban saida ya fada mata maganganun da suka sakata tashi cikin damuwa akan yarsa dan hakanne ta tashi aikin da bata taba sabawa dashiba. Saida falaq ta gama komai itace ta kaita school din ta dawo. A gajiye take jinta dan haka ta kwanta ko baccin isashe bata wani samu ba lokacin tashi saura mintina 40 ta nufi school din itada Fiddausi suka jira aka tashi ta dawo dasu gida. Sallah da abinci kadai sukaci ta sake ficewa kaita islamiyya sbd malaminta bayanan yayi tafiya dan haka makarantar ake kaita kafin ya dawo. Ganin bazata iya dawowa gida ta komaba zaunawa tai a makarantar har aka tadasu sika dawo gida. Wannan karan itace mugun zazzabin wahalar da bata sababa ya kama Idanuwanta sunyi wani irin laushi gwananin tausayi amma ta daure ta hana su Dad ganewa bare suyi magana. Washe gari ma haka ta qare a cikin wahalar dare nayi zazzabi yansake rufeta daqyar ta iya tashi sallan asuba. A cikin kwanaki kadan ta koma abar tausayi ko Fiddausi tsananin tausayinta takeji gashi umarni ne daga AZIZ din itace zata kula da falaq tinda itace ta saka aka kawota. Ita kanta falaq tsananin tausayin Jannah din wadda ta fara rama a kwanakin take sbd tsananin wahalar da bata sababa ta fara yimata yawa gashi taqi denawa. Duk inda damuwa da qunci suke sun cike Familyn zaadens sbd sunaji suna gani Jannah din take wannan wahalar sunyi sunyi ta dena ta kasa denawa, Har sabuwar mota takanas dad ya siyawa falaq tareda drivers dan a ringa kaita Jannah ta huta amma sam AZIZ LIMBA yace baya wasa security din 'yarsa sbd baisan drivers dinba adai bari Jannah din taci gaba kafin ya dawo. Maganar dawowansa ma jin Dad yayi hankalinsa ya tashi ya shiga damuwa sosai akan tarewanta sbd tsoron irin wannan wahalar zataje kawai tasha dan haka sukaji auren yafara fita ransu tin baa tareba. Mimi ma datake yawan video call da ita ganin yanda taga Jannah din ta koma sai taji kuma ta shiga damuwa sosai da tausayinta. Duk familyn zaadens babu wanda yake jin dadin ganin halinda jannah take ciki gashi sam taqi nuna damuwa ko gajiyawa duk da yanayinta ya nuna hakan sbd duk dare da zazzabin wahala take kwana. Ammar ma tinda yaga jannah so daya yaji hankalinsa ya tashi da son dawowa dan haka suka tattaro suka dawo batareda sun sanar ba. Da yamma su Mimin suka dawo lokacin jannah na kitchen tana tareda Fiddausi suna aikin cake da falaq tace zataje school dashi. Yau tasha wuya sosai sbd tinda ta tashi da asuba bata komaba tana kan yawo da aiki. Ko abincin kirki bata ciba gashi Class party ne zaayi a school din. Jin ana murnan dawowansu Mimi ta goge hannunta da qaramin towel ta fito tana nufo babban palonsu. Ammar dayake sako kai a palon akanta idanuwansa suka fara sauka zuciyarsa tai wani irin daukewa wani irin nauyi me sanyi yana danne kirjinsa batareda ya dauke idanuwansa akantaba yana kallo. Itama shi din idanuwanta suka fara sauka akansa ta zuba masa ido Yayi kyan gani ya samu nutsuwa ba kamar yanda yabar gida ba. Numfashi me sanyi ta sauke tana dauke idanuwanta akansa tana maidawa kan Mimi tareda sake murmushin farin cikin ganinsu ta nufi Mimin da gudu ta rungumeta tanajin zuciyarta tana karyewa tace "Mimi nayi kewanku dan Allah kada ku sake tafiya ku barni" Mimi da bataji dadin ganinta a yanda ta ganta ba murmushin karfin hali ta sake tana rungumeta tace "Ina zamu dake kina matar wani" Basar da zancen jannah tai tana dawo da kallanta kan Ammar da har lokacin ita yake kalla tace "Barka da dawowa Ammar Zad" Murmushi me kyau ya sake mata yana cewa "Thank you Jannah Zad" Maheer ne ya qaraso ya rungume Ammar din yana cewa "Welcome back Bro" Amsawa yayi yana rungumesa batareda komai a ransa ba yace "Yaya muka sameku? Anny ma Mimi ta rungume tana musu barka da dawowa kafin suka qarasa ciki gabaki dayansu. Falaq ma fitowa tai da murnanta taiwa Mimi oyoyo tana rungumeta. Cikeda kauna Mimin ta rungumeta tana cewa "Falaq yaya kike? Yaya baqunta? Murmushi tai tana amsawa tana sake musu sannu da zuwa. Fiddausi da sauran yan aikin gidan fitowa sukai suna musu barka da dawowa. Da daddare bayan kowa ya nutsu ya huta suna kan dining suna cin abinci Jannah data iso tareda falaq din kallansu kowa yayi cikeda tausayin Jannah, Zama sukai suka fara cin abincin Ammar ya kasa samun nutsuwan ganin abincin da Jannah zataci dan haka da kansa ya miqe ya sake serving nata wani abincin sbd gaba daya ta zabge kamar bata cin abinci. Cikeda kulawa yace "Kici wannan you don't look good" Thank you" tace tana murmushi. Falaq data kasa cin abincinta tana kallansa jin tai gabaki daya cikinta ya cika dan haka fasa cin abincin tai ta miqe tabar dining din. Babu wanda yace komai hakama dukkaninsu jannah suka zubawa ido suna kalla. Batace komaiba itama hakama bata dagoba tsawon mintina 2 sai sukaga ta miqe tana bin bayan Falaq din. A tare dukkaninsu suka sauke ajiyan zuciya mara dadi banda Ammar da baqin ciki da takaici suka rufesa ya miqe yabi bayan Jannah din dakinta. Tana shida dakin daidai fuskansa na bayyana akan screen din ipad din Falaq data saka kiransa video call. Ta bayanta jannah din ta bayyana Ammar na bayanta zai miqa hannu ya riqota Muryan AZIZ din ya bayyana yana ambatar sunan falaq Dukkaninsu Screen din suka kalla Ammar na kasa motsawa hakama jannah din falaq ma juyowa tai ta kallesu ganin inda Daddyn nata yake kalla taga Jannah da Ammar a tsaye. #MAMUH ZAFAFA BIYAR KALBIM 500 mamuhgee A DUNIYATA 500 Huguma AJIYA A DUHU 500 Billyn Abdul KIRJIN ME HANKALI 500 Miss xoxo Pay at 0022419171 AccessBank Maryam sani gummi Shedan biya 09033181070 Or mtn vtu at 09032345899*_KALBIM_* _Mamuhgee_ 64 *UMMU_MAHNOOR LUXURIES* (Best luxuries shop) 08034469681 08135142610 Aslm Alaikm ina kuke masu neman luxuries na kayan alfarmar kece raini? Ina masu son su saka sitirar alfarma ta zamani ta manyan mata masu aji da zaa kalleki kallo daya asan sitirar alfarma e kika saka? Shin kunsan me ake nufi sa kayan asalin yan gayu da nuna gayu? Sitirar Alfarma kikeson sakawa? Sitirar da kike ganin manyan mata da ita? Sitirarda zakiyi gayun sallah dake da yaranki a dauka waje kikaje da kanki kika siyota? To kizo ga damarki ta sameki sbd UMMU_MAHNOOR LUXURIES ta kawo miki sauki har gida, Karkice se masu kudi ke iya siya har kema me yar dama zaki samu naki da saukin kudi kuma best quality da kalar zamani data yan gayu, Nidai Mamuh nace duk wadda ke son a buga gayun sallan bana da ita da 'yayanta to tazo gurin UMMU_MAHNOOR LUXURIES tai siyayyar sallanta harma zuwa gaba dan nasan zakuji dadi da fahimtar abinda nake fada akan kayanta💯💯 Abubuwan da zaki samu a gurinta with the best quality na wayayyun mata masu aji yan gayu sune; Atampopi Laces Shadda Materials Shoes Bags Veils Trolleys Jewellerys Oil perfumes Numbers 08034469681 08135142610 Handles Instagram @ummu_mahnoor_luxuries TikTok username @ummu_mahnoor_luxuries Facebook ummu_mahnoor_luxuries ************* Dauke idanuwansa yayi akansu tareda maidawa akan 'yarsa yana kallanta ya bude baki yana jingina bayansa a sofan dayake zaune cikin free size balenciaga shirt da three quarter fuskansa ta qara haske sosai a natse yace "Yaya nake ganin fuskanki da damuwa? Akwai abinda yake damunki? Juyawa tai ta saci kallan Ammar dayake bayan jannah zuciyarsa na tafasa ta dawo da kallanta kan jannah datai sanyi Sai taji tausayinta me tsanani ya rufeta dan haka ta dawo da kallanta kansa ta girgiza kai alamar ba komai. Ammar ya jefawa kallan dayafi kama dana mutum ne ko aljan kafin ya dawo da kallansa kan Jannah din batareda ya ambaci sunanta ba yace "Meya sameta? Nunfashi ta fara saukewa a sanyaye kafin ta dago ta kallesa tana danne damuwarta tace "I dont know kawai ta fasa cin dinner ne" "Akwai abinda kukai mata ne datai loosing appetite nata, So me kike jira da bazaki mata dubarn da zataci ba? Kunason ta kwana da yunwa ne? Idan akwai specific abinda taji tanason ci a nema mata a bata mana, Komai sai anfada miki yanda zakiyi¿ You ar unbelievable...." ya qarasa fada yana kashe wayarsa. Ammar daya mutu a tsaye sbd tsananin mamaki da tashin hankali da baqin cikin baisan lokacinda ya kalli jannah da zuciyarta ke mata ciwo ba yace "Is he okay? Like is this Guy normal? Yasan waye jannah zad kuwa? Yana wasa da rayuwarsa ne? Haka yake treating naki duk tsawon lokacin nan? Juyawa Jannah tai batareda tace komaiba tabar dakin sbd Falaq sam bata kaunar ayi maganar Daddynta da daga murya bare rashin girmamawa ko cin fuska haka dan haka ta fice dan tasan zai biyota ne. Suna isowa babban palo ta dakata tareda juyowa ta kallesa ta bude baki cikin damuwar datake ciki tace "Meye kakeyi hakan a gaban Falaq?zata iya kwana tana kuka and hakan zai iya sakata wani ciwon da zai..... kasa qarasawa tai tana hadiye sauran zancen da damuwarta idanuwanta na sauyawa. Cikin zafi da baqin ciki mai tsananin gaske Ammar ya daga murya yana cewa "Idan yana taqama da yana tsananin kaunar 'yarsa bai hadata da komai da kowa ba to mun dade da wucesa a gurin sbd har abada bazai iya abinda mu mukai akanki ba, Me zakiyi da aurensa idan har tin kina gida a gabanmu yana miki hakan? Meye a cikin aurensa? Meye zakiyi dashi? Meyasa kikai shiru kina hadiye wulaqancinsa? Why,why Jan? Wani irin nauyi da tsananin ciwo ne ya toshe zuciyarta hawayen datake riqewa suka gangaro mata ta rintse idanuwanta tana jefawa zuciyarta itama Why ta kamu da tsananin sonsa irin hakan, Da zata iya bawa Ammar amsa data fada masa menene yake azabtar da ita. Gabaki daya su Dad da hayaniyar ta kawosu palon tsayawa sukai suna kallan hawayenta dake sauka zuciyoyinsu na radadi da ciwo tareda jin auren kwata kwata ya fita ransu a yanxu yancin yarsu kawai sukeso. Bude idanuwanta da sukai jajir tayi taga irin kallan da suke mata ta juya batareda ta tsaya jin abinda zasu fada ba ta nufi kitchen sai ganinta sukai ta fito dauke da tray ta wuce zuwa dakinta. Saleem ne ya isa gurinta ya karbi tray din yana cewa ta kawo ya daukan mata cikeda kulawa da kaunarta me tsanani. Dad bai iya cewa komaiba palonsa ya wuce Maheer ma nasu palon ya wuce Anny na gefensa riqe da hannunsa. Mimi Ammar dayake jin kaman zai kama da wuta ta nufa ta kama hannunsa tana maidasa dining ta zaunar tanason yaci abincin amma sam bai iya ci ba idanuwansa sunyi wani irin jajir maganganun da LIMBA ya fadawa Jannah suna yawo a kunnuwansa. Suna isa daki falaq suka tarar a zaune idanuwanta sunyi jajir alaman kuka tayi tana ganinsu ta zubawa jannah ido da itama idanuwanta suka nuna kukan tai Take taji jikinta ya sake sanyi. Tashi tayi ta nufo Jannah din sedai kafin tace komai jannah ta kama hannunta tana kokarin sauya yanayinta ta zaunar da ita a sofa tana cewa "Zo kici abinci" Girgiza kai falaq tai tana cewa "No kema bakici ba" Saleem daya ajiye tray din akan table din gabansu cikeda kulawa garesu su biyun yace "Dukanku zakuci abincin ai yanzu dolenku" Kallansa Falaq tai tana sanyi tace "Idan jan zataci zanci, Idan bazata ci ba nima bazanci ba" Murmushi ya sake yana kallan falaq din kafin ya kalli jannah yace "Your baby tace bazata ci ba idan bazaki ci ba so Ms Jan limba me kikace?? Kallan falaq din tai tana sauke ajiyan zuciya ta miqa hannu tana cewa "Zanci" A tare sukaci abincin shikuma saleem din yan kokarin sauya yanayinsu har suka sake suka dawo walwala da dariya. Har kusan 10 da mintina yana dakin har saida ya tabbatarda sun gama dawowa cikin farin ciki tukuna yai musu saida safe ya fice. Harya fito duk tsawon wannan lokacin Mimi da Ammar na palo zaune zuciyoyinsu ba dadi dan haka ya sanar dasu komai ya daidaita sun dawo walwalwansu duk su dukan. Yar ajiyar zuciya Mimi ta sake tana juyawa ta nufi dakinta Ammar kuwa ko sunan Falaq din jin yayi baya kaunar sake ji dan haka shima barin palon yayi ya nufi bangarensa yana jin kaman ya dawo da rayuwarsu baya ya goge shigowan AZIZ LIMBA rayuwarsu ya hana haduwansu dashi kwata kwata. Wanka Falaq tafara yi tai shirin bacci ta hau gado ta dauko ipad dinta lokacin jannah na cikin toilet gurin wanka ta saka kiran Daddynta. Daman kiranta zaiyi sbd tabbatarda taci abinci bata kwana da yunwa ba. Zaune yake a bedroom dinsa shima sanye da fararen kayan bacci ya dora Cardigan akai me girma sbd yanzu ya gama conference meeting da wasu presidents dinsa na U-LIMBAs companies. Cikin kulawa da sakewa tareda kauna take sakin murmushinta me kyau sbd yasan ta dake bata cikin damuwa dan kada yayiwa Jan dinta fada tace "Daddy naci abinci tareda My jan kuma bana cikin Damuwan komai yanxu" Hancinta ya kalla fuskan Ummitansa na bayyanar masa akan fuskanta ya saki wani Kyakkyawan murmushi yace "Thank god Besty zaiyi baccin nutsuwa kenan tinda falaq Aziz taci abinci" Dariya tayi sosai kafin tace "Daddy pls ka dena yiwa my jan fada ni banaso, Banason tayita kuka, Koyaushe kayi fada sai tayi kuka sosai, Ka ringa rarrashinta nakeso kaman yanda kakemun, Kaji??? Bakinta dayake maganar ya kalla kafin ya basar yana cewa "Ki fadamun abinda ya sameki tukuna" Mantawa tai da tace bazata sake nuna masa damuwanta anan ba ko fada masata gyar zama tana turo baki tace "Daddy ni banason Ammar Zad yana kula Jan tinda ai yanxu Jan din Daddyna ce ba tasa ba, Yanata kallanta baya kallan kowa sai ita, Shine ana dinner ya ringa zuba mata abinci yana kokarin bata kamanma fa zai bata a baki, I hate to see him near our Jan shiyasa nayi fushi na fasa ci kuma shine ya biyota bar daki kuma yanata fada, Daddy i don't like him sbd Jannah ta Bestyna ce kadai... Inda taga yayiwa kallo daya ya dauke fararen idanuwansa ya sakata juyawa ta kalla Jannah ce ta fito daga wankan sanye da bathrobe blue yar qarama da batada wani tsayi sosai. Saukowa tai daga gadon da sauri ta nufi gaban mirror din da jannah ta zauna ta ajiye ipad din gaban mirror gabaki dayan jannah ta bayyana a cikin screen din hatta siraran cinyoyinta dake daukan idon haske da lafiya da hutu. Ba zato jannah ta gansa a gabanta Da sauri ta kallesa ya dauke idonsa yana kallan Falaq data tsaya bayanta yace "Ki kwanta time na baccinki ya wuce saida safe.." Saurin hanasa kashewa falaq tai tana cewa "Besty Kaikace idan nafada zakamun abinda nakeso, Inason ka rarrashi My jan she s sad deep down" Saurin kallanta jannah tai tana kasa kallansa sbd tanason miqewa Amma miqewanta zai qara bayyanarda jikinta ne. Falaq kallan jannah tai tace "Jan karkice bakyaso my Daddy ya iya rarrashi zakiji bazaki sake shiga damuwaba" Idanuwanta ta dago ta dora akan screen din taga ita yakewa wani kallan daya sakata jin zufa na gangarowa daga wuyanta zuwa cikin rigar wankan jikinta... Harbawa zuciyarta keyi sosai har yana iya gani ta jikin rigarta. Baice komaiba da idanuwansa ya ringa azbtar da ita sbd yana ganin yanda kirjinta ke tsananta bugu... Zufan daya gangaro daga wuyanta zuwa kirjinta yabi da kallo yana maganganun Falaq na dawo masa. Falaq kuwa qaramin towel ta dauko tazo gurin jannah din data bari hango zufan datai yana mata tsiyaya duk akwai ac. Tana zuwa hannunta daya ta dora ta janye rigar zuwa qasa tana dora towel din.... Dauke idanuwansa yayi akanta tareda kashe wayar gaba daya sbd yanda ba zato falaq ta zame mata rigar saida ya bayyana jikinta sosai har gurin saman kirjinta. Rawa hannuwan Jannah din suka fara tai saurin karban towel din tana jin bugun zuciyarta na tsananta tai saurin daukan remote ta qara Ac ta zauna bakin gado ta samu bugun zuciyarta ya daidaita kafin ta miqe ta shirya batareda ma tayi wani shafe shafen turarukanta data sababa. Falaq kuwa cewa tai "My jan karki damu Daddy na dawowa zamu koma gida acan zan saka ya ringa lallabaki kaman ni, Mama ma tana sonki sosai zata ringa rarrashinki ta sakasa ya ringa yi shima" Murmushi kawai Jannah din ta sake tana cewa "Naji,kiyi adduar kiyi bacci gobe akwai school karki manta" Itama murmushin tai tana addua ta rife idanuwanta take bacci y dauketa. Ita kuwa tana rufe idanuwanta nasa idanuwan take jin suna mata yawo a koina da kallansa daya kusa bata attack. Washe gari kan lokaci sukai shirinta kafin kowa ya tashi takaita ta dawo ta shige kaman bata fitaba ta kwanta baccin safe itama. Sai 10 mutan gidan suka fito itama hakanan ta tashi batareda baccin ya ishetaba tai wanka ta fito zuwa dining. Ganinta yau din a natse ba kamar sauran kwanakin datake neman haukacewa sbd wahala ba ya saka suka samu nutsuwa harma sukai breakfast din cikin jin dadi da farin ciki. Itama sakewa tai ta nuna bata cikin damuwar komai. Lokacin tashi na yi yau saleem ne yaje da kansa ya dauko Falaq daqyar ya lallaba jannah ta hakura yaje ya daukota sbd ita ta huta. Falaq ma ganin saleem ne bata damuba sbd itama tana son jannah ta huta hakama Fiddausi tausayinta take sosai dan haka sai saleem da Maheer suka karba kai falaq din qarfi da yaji wani lokacin harda Ammar sbd dukkaninsu sunason Jannah ta huta gashi Kai tsaye AZIZ LIMBA ya nuna koda wasa kar a hada 'yarsa sa driver hakanne yake saka jannah jin tsoron barin falaq din a hannun kowa sai da sukaga tana neman lalacewa a gabansu suka karba aikin kai falaq din da daukota akan lokaci kaman marasa aikin yi duka ba dan suna so ba. #MAMUH ZAFAFA BIYAR KALBIM 500 mamuhgee A DUNIYATA 500 Huguma AJIYA A DUHU 500 Billyn Abdul KIRJIN ME HANKALI 500 Miss xoxo Pay at 0022419171 AccessBank Maryam sani gummi Shedan biya 09033181070 Or mtn vtu at 09032345899*_KALBIM_* _Mamuhgee_ 65 *UMMU_MAHNOOR LUXURIES* (Best luxuries shop) 08034469681 08135142610 Aslm Alaikm ina kuke masu neman luxuries na kayan alfarmar kece raini? Ina masu son su saka sitirar alfarma ta zamani ta manyan mata masu aji da zaa kalleki kallo daya asan sitirar alfarma e kika saka? Shin kunsan me ake nufi sa kayan asalin yan gayu da nuna gayu? Sitirar Alfarma kikeson sakawa? Sitirar da kike ganin manyan mata da ita? Sitirarda zakiyi gayun sallah dake da yaranki a dauka waje kikaje da kanki kika siyota? To kizo ga damarki ta sameki sbd UMMU_MAHNOOR LUXURIES ta kawo miki sauki har gida, Karkice se masu kudi ke iya siya har kema me yar dama zaki samu naki da saukin kudi kuma best quality da kalar zamani data yan gayu, Nidai Mamuh nace duk wadda ke son a buga gayun sallan bana da ita da 'yayanta to tazo gurin UMMU_MAHNOOR LUXURIES tai siyayyar sallanta harma zuwa gaba dan nasan zakuji dadi da fahimtar abinda nake fada akan kayanta💯💯 Abubuwan da zaki samu a gurinta with the best quality na wayayyun mata masu aji yan gayu sune; Atampopi Laces Shadda Materials Shoes Bags Veils Trolleys Jewellerys Oil perfumes Numbers 08034469681 08135142610 Handles Instagram @ummu_mahnoor_luxuries TikTok username @ummu_mahnoor_luxuries Facebook ummu_mahnoor_luxuries ************* Break na sati biyu su falaq suka samu a school wanda kaf familyn zaadens babu wanda baiyi farin ciki da hakan ba sbd jannah zata huta suma zasu huta daga aikin da bana Allah ba. Hutu yanzu jannah take samu duk dan haka itada Falaq din basa fita koina sai hutu a gida da wasa da farin ciki sosai. Tinda falaq tazo gidan babu asubar da baya kira a waya dan haka tin tana jin wani iri harta fara sabawa kiransa na shigowa take tashi ta tada falaq sallah. Kowanne dare ma yana video call da yarsa kafin su kwanta sedai tana iya kokarinta na kaucewa ganinsa dan haka suka kwana biyu batareda sun sake ganin juna ba. Ta bangaren Ammar kuwa kai tsaye ya fito ya nuna bazai taba dena ji da jannah ba ko dena kulawa da ita ba kaman yanda ya saba sbd yanzu ne ma yake jin ya kamata ya tsaya tsayin daka akan ganin ta dawo hannunsa sbd bazata taba farin ciki da daraja a gurin limba ba, Hakama su Dad a yanzu suna bayansa rabuwar auren sukeso dik da kuma ta wani bangaren suna shakkar rabata da abinda takeso dan haka tinaninsu ya kasu kashi biyu. Maheer kuwa sosai ya maida hankali ya kutsa akan harkan businesses na Limba dan su samu kama abinda zasu kama dazai dawo musu da duka abinda suka rasa su sake rising da kansu dan hakanne kawai zasuyi su nuna masa karfi su raba jannah da aurensa dan yanzu sunsan idan ba shine yaga dama ya saketa ba kome zasuyi bazai saketan ba sbd baa juyasa yanda aka ga dama. ******Jannah ta dawo jannah dinta Mimi ma sosai take tattalinta yanzu hakama kowa familyn, Duk yanda suka gaji da zaman falaq a gurinta sbd wahalar datake akanta basa fatan AZIZ LIMBA ya dawo a yanxu sbd dawowansa na nufin tarewanta wadda yanzu suke jin shakka dan haka suka zabi zaman falaq din anan indai hakan na nufin jannah dinsu zata zauna gida bayanan. Ta bangaren falaq kuwa abu dayane yake saka zuciyarta zafi da jin gajiya da zaman gidan yanzu shine yanda kusancin Ammar da jannah din yake, Kishi takeyiwa Daddynta me tsanani zafin gaske dan zafi sosai take ji taga Suna sakewa da juna suna murmushi Ammar na Bayyanarda yanda yafi kaunarta fiyeda kowa a gidan. Wannan ke sakata jin kaman zuciyarta zata fashe dan haka ta matsawa Daddynta ya dawo tana fada masa duk abinda yake faruwa. Ba yace mata komai sedai kawai yayi kaman baijiba suyi wani maganar ya kashe waya. Falaq din dena walwala tai a gidan ta rage zuwa cin abinci a cikinsu sedai Fiddausi ta kawo mata daki, Jannah data lura da hakan sai ta ringa lallabata batareda tasan meyake damunta ba sbd bata fada mata abinda yasaka bata fitanba. Ganin taqi sakewa kwana biyi yau suna tashi suna gama breakfast tace "Zamuje beauty palour a gyara miki kanki, Zakije?? Kallanta falaq tai tana sake fuska sosai tace "Eh zanje,zamu zauna acan sai dare zamu dawo banason wuni a gida" Murmushi jannah tai tana cewa "Meyasa Falaq Aziz batason wuni a gida? Akwai abinda yake damunki? Kallanta falaq tai tana cewa "Banason ganin kowa yana rabanki idan ba Daddyna ba haushi nakeji, Kema kuma kin dena son Daddyna" Kallan mamaki jannah tai mata tace "Heyy Falaq me kike fada? Shiyas kika saka kanki a damuwa kwana biyu? I dont like seeing you like this my baby" Bata fuska falaq tai tana cewa "Meyasa yanzu kika dena son Daddynah??? Shiru jannah tai sbd zancen ya fara zama serious coz ta dauka shirmen falaq dinne amma ganin yanda har idanuwanta suka ciko da hawaye ya sakata kallanta tana kokarin magana falaq din ta katseta da cewa "Kin dena son Daddyna da gaske Ammar Zad kikeso?? Janyota jikinta falaq tai tana girgiza mata kai ahankali tana kasa cewa komai.. Hawaye na gangaro mata zata goge ta hango Ammar yana shigowa palon tareda Mimi da Maheer ta sake tsiyayo wasu hawayen na gudu tace sai jannah ta fada mata meyasa ta dena Son daddynta. Rasa yanda zatai jannah tayi ta kalli falaq din dake hawaye sosai ta bude baki cikin sanyi da nutsuwa tace "Haryanzu Shine a zuciyana duk da nayi kokarin cire hakan na yakice na yar amma na kasa, I endured and tolerated everything sbd nakasa cire abinda yake zuciyana so pls karki saka abubuwa sumun nauyi da wannan tambayan naki,pls Falaq" Ammar dayayi mutuwar soja daga inda yake Mimi ta kalla zatai magana Maheer ya juya yabar gurin yana sauke numfashi me zafi. Mimi kuwa falaq ta kalla wadda ta rungume jannah cikeda farin ciki tana cewa "My jan nayi miki alkawarin Bestyna zai so ki fiyeda hakan insha Allah, Mu shirya mu fitan to" Ammar juyawa yayi da sauri yabar palon baya gani sosai duk da kansa ya kasa fahimtar asalin abinda jannah ke nufi da kalamanta dan hausa gaba daya jin yayi ta bace masa. Mimi ce tai karfin halin tsayawa tana sake fuska ta dan shiga firarsu kafin suka je shirin fita. Driver suka fita dashi su hudu zuwa Saloon din, Jannah din da falaq sai Anny da Fiddausi jakar hannun Falaq. Vip card ne dasu a tsadaddiyar Palour din dan haka suna isa suka wuce sama ana musu barka da zuwa gurin tsit a tsare kaman baa Nigeria ba. Dayake daga falaq din har Fiddausi ma datake matsayin me aiki har inda yafi nan din suna zuwa a kasashe dan haka basu wani damu ba. Gyaran kai da qafa da fata da duk sauran gyara hankali kwance, Anan sukai lunch na lafiyayyan tsadaddan abinci sbd akwai komai a cikin gurin kome kakeso zakai order ne a kawo maka. Farin ciki falaq take cikinsa sosai suma kusan duka a cikin farin ciki da walwala sukai wunin guri. Daga can wani Mall suka biya suka siya wasu abubuwan hadda Sabbin Nighties suka siya na matching kala jannah da falaq din. Siyayyar masu abin duniya sukai ba yawa sosai se kudi hakama wani abin kaman baida amfanin siya. Sai yamma sosai suka dawo gida lokacin ana ma kokarin shiga sallan magrib. Wanka sukai tareda sallah tukuna suka fito jannah na gaba sanyeda doguwar riga mara nauyi datake rawa ta dan lafe a jikinta ba dankwali akanta tana duba chat a wayarta yunwa take ji ta nufo palo Mimi da Saleem zaune yana nuna mata wani sako a wayarsa Ammar na kan one sitter yana duba abu a ipad dinsa kamar ma Meeting yakeyi sbd yanda ya nutsu ya maida hankalinsa sosai. Anny ce ta fito itama tana waya hannunta riqesa robar ruwan datasha ta rage ta zauna gefen Mimi. Falaq ce a bayan jannah tana duba wayarta data bari gida. Misscall din Uncle sayd ta gani da numbernsa ta Nigeria da sauri ta sake dubawa farin ciki na mamayeta kafin tai magana qamshin daya shiga hancinta ne ya sakata kallan kofa da sauri tana cewa "BestDaddy" Dad ne a gaba da maheer suka shigo palon sai gasa ya shigo a natse kwarjinsa kwarjinsa aura dinsa na cike palon tareda qamshinsa me tsananin sanyi da aji. Sanye yake cikin black Alexander Mcqueen ya qara wani irin haske da fresh.... Cikin tsananin farin cikin da batasan iyakarsaba falaq tayi kansa da saurin gaske tana ambatar sunansa. Tin bata qarasoba ya ware mata hannayensa ta fada da karfi tana rungumesa. Cikeda kaunarta dayake maya me sanyi ya zagayeta da hannuwansa duka biyu yana cewa "Heyy my angel" Murmushin karfin hali kowa keyi suna bayyanarda farin cikin ganinsa banda jannah data kasa motsawa daga inda take. Ammar kuwa ko dagowa baiyiba yaci gaba da abinda yake yana jin nauyi na danne kirjinsa. Sakinsa tai tana cewa "Daddy ka dawo baka fada mana ba" Sake rungumesa tai tana jin kaman zata fashe da farin ciki. Sakinsa ta sake da sauri ta juya taje gurin jannah ta kamo hannunta ta janyo da karfi ta turata gabansa ba tsammani ta hade kirjinsu tana rungume jannah din ta baya sika fada kansa dukansu kirjinta na qarasa mannuwa da nashi batareda zatonsu ba su dukan dan haka saura kadan numfashin jannah yabar kirjinta har batasan lokacinda ta qanqame gefen rigarsaba a tinaninta rigarta ce tana rintse idanuwanta da karfi sbd fargaba. A lokacin ne Ammar yaji gabaki daya ya rikice baya gane komai na abinda yakeyi ya dago idanuwansa da sukai jajir ya sauke akan AZIZ din wanda ko inda yake bai kallaba ya saka hannu ya zare jannah din daga jikinsa. Falaq saurin ture hannunsa tai tana cewa "Daddy nida Jan munyi missing dinka sosai, Ka dena turemu" sake qanqamesu duka tai tana sake jin farin cikinta na yawa tace "We love you Daddy" Sayd dayake bayansa fuskokin zaadens din ya kalla daya bayan daya yaga yaqe kawai sukeyi babu alamar har zuciyarsu farin cikin yake. Hannuwansa ya saka duba biyun ya zagayosu jikinsa dakyau yana sauke idanuwansa akan Ammar dayake jiqewa da zufa. Ita kuwa dagowa tai ta kallesa cikin fargaba da bugawan zuciya jin irin rungumar da yayi musu. Shima ita ya dawo da kallansa akanta cikin tsananin bugawan da tasa zuciyar tayi sbd jin tsananin bugun zuciyar datake kirjinsa a nasa kirjinsa yana sauka. Jin yayi zafi da sanyi masu tsananin kargi suna rufesa lokaci daya idanuwansa suka kasa daukewa daga kanta a karan farko yana jin bugun zuciyar Ummitah a kirjinsa. Janyeta yayi da sauri daga jikinsa yana hana kowa ganin idanuwansa ya kalli jannah din da itama da sauri taja baya tana komawa gefen Dad dinta ta riqe hanunsa zuciyarta na bugawa sosai ta kasa dagowa ta kallesa. Saleem ne yayi saurin tasowa yana masa barka da dawowa sai a lokacin ya dago ya kallesa yana amsawa a natse kafin ya gaisa da Anny ya kalli Mimi suka gaisa a gajarce sbd ba sabo a tsakaninsu. Ammar da yake kokarin hana yanayinsa bayyana a gaban AZIZ LIMBA miqewa yayi yana barin palon batareda kowa ya luraba sai shi limba din. Dad da daman sun gaisa tare sukai magrib ma yace su qarasa palonsa. Wucewa sukai har lokacin falaq na riqe da hannunsa bakinta yaqi rufuwa. Jannah ma tana riqe da nata hannun Dad din. #MAMUH ZAFAFA BIYAR KALBIM 500 mamuhgee A DUNIYATA 500 Huguma AJIYA A DUHU 500 Billyn Abdul KIRJIN ME HANKALI 500 Miss xoxo Pay at 0022419171 AccessBank Maryam sani gummi Shedan biya 09033181070 Or mtn vtu at 09032345899*_KALBIM_* _Mamuhgee_ 66 *UMMU_MAHNOOR LUXURIES* (Best luxuries shop) 08034469681 08135142610 Aslm Alaikm ina kuke masu neman luxuries na kayan alfarmar kece raini? Ina masu son su saka sitirar alfarma ta zamani ta manyan mata masu aji da zaa kalleki kallo daya asan sitirar alfarma e kika saka? Shin kunsan me ake nufi sa kayan asalin yan gayu da nuna gayu? Sitirar Alfarma kikeson sakawa? Sitirar da kike ganin manyan mata da ita? Sitirarda zakiyi gayun sallah dake da yaranki a dauka waje kikaje da kanki kika siyota? To kizo ga damarki ta sameki sbd UMMU_MAHNOOR LUXURIES ta kawo miki sauki har gida, Karkice se masu kudi ke iya siya har kema me yar dama zaki samu naki da saukin kudi kuma best quality da kalar zamani data yan gayu, Nidai Mamuh nace duk wadda ke son a buga gayun sallan bana da ita da 'yayanta to tazo gurin UMMU_MAHNOOR LUXURIES tai siyayyar sallanta harma zuwa gaba dan nasan zakuji dadi da fahimtar abinda nake fada akan kayanta💯💯 Abubuwan da zaki samu a gurinta with the best quality na wayayyun mata masu aji yan gayu sune; Atampopi Laces Shadda Materials Shoes Bags Veils Trolleys Jewellerys Oil perfumes Numbers 08034469681 08135142610 Handles Instagram @ummu_mahnoor_luxuries TikTok username @ummu_mahnoor_luxuries Facebook ummu_mahnoor_luxuries *********** Ko zama basuyiba Anny ta shigo tace angama shirya dining suka juya zuwa dining din duk da babu abinda zaici amma sbd Dad din daya sake cewa yaje din da falaq data takura akan sai yana gurin zataci suka nufi dining din. Maheer ne yaja masa kujera ya zauna cikin basa yar girmamawa matsayin baqonsu kuma sirikinsu. Zama falaq tayi kusa da daddynta jannah kuma na gefenta shikuma Ammar yana gefen jannah din. Fiddausi ce tai serving nasu abinci gabaki dayansu sbd kwana biyu ta shiga cikin masu aikin gidan kuma sosai sukejin dadin komai nata akan nasu masu aikin da ake biya da tsada. Jannah data kasa sakewa taci abinci Ammar ne ya kalleta yana daukan serving spoon zai zuba mata chicken soup akan abincinta dayasan tana so maganar AZIZ LIMBA ta ratsa shirun gurin a natse hankali kwance da cewa "In the next 40 min zan tafi tareda falaq Aziz da......kallan Ammar yayi kafin ya kalli jannah da bata dagoba yace "Da Matar da aka bani......" Serving spoon din hannun Ammar kubucewa yayi daga hannunsa ya fada cikin soup din tayi baltsin daya sakasa saurin dora hannunsa akan fuskan falaq dake gurin daidai tareda hannun jannah din hannunsa ya sauka nata a qasa nasa a sama. Maheer da Dad kuwa a tare suka sarke da abincin da suke ji suna dagowa kallansa. Anny tai saurin bawa Maheer ruwa Mimi ma Dad din ta bawa hannuwanta na dan rawa tana kokarin boye nata tashin hankalin. Jannah ma ahankali ta dago ta kallesa idanuwanta na cikowa da hawaye. Shi kuwa kaman bashine yayi maganarba ya kalli falaq da wani irin farin ciki ya sake ciketa ta riqe hannunsa dana jannah tana cewa "Thank you BestDaddy" Dad ne daya gama tari ya kallesa yana boye damuwarsa yace "Da sauri haka babu shirin komai? Ko zaka bari zuwa nan da kwana biyu ta shirya a natse" Zubawa dad din idanuwansa yayi baida niyar basa amsa saida Ammar ya kasa hakuri yace "Daman ai hakan ya kamata abari komai ya tafi a natse" Batareda AZIZ ya kallesaba ya kalli Dad yace 'idan tana buqatan qarin kwana biyu zan qara mata sati daya Amma Dr Ammar Zad ne zai kaita da kansa, Idan ya yadda zai kaita har cikin LIMBAs to shikenan ta qara sati daya" Kallan Ammar kowa yayi ana jiran amsarsa shikuwa AZIZ din ya zubawa ido zuciyarsa kaman zata fashe da tsananin baqin cikin jin shi yakeso yakai Jannah da kansa gidan wani. Dad ne ya dauke kallansa daga Ammar din yana cewa "To ai wannan ba damuwa bane tinda daman qanwarsa ce yanada haqqin kaita gidan mijinta dan haka ba damuwa hakan yayi" Abincin dayake bakin jannah dinne ya wuce mata da karfi tana daukan ruwa a cup tasha ahankali ya wuce. Ammar ma jin yayi abincin dayake cikin bakinsa ya koma masa kaman madaci ya hadiye daqyar tareda shan ruwa. Anny kuwa cikin farin ciki itama take dan haka itada saleem ne kadai da falaq sukaci abincinsu hankali kwance akan dining din. Falaq na gamawa ya tashi tareda ita suka bar dining din dan shima kadan yaci yabar musu kayansu. A palon Dad suka zauna shida Dad din da daddy mahmoud da maheer sunata firar business da wasu abubuwan. Ita kuma falaq tana daki Jannah da Fiddausi na hada kayanta dan Daddynta zatabi yau kam sai gida batajin zata iya bacci bayan tasan Daddynta na gari. 9 suka fito tana riqe da hannun jannah tanajin kewanta tin bata tafi ba. Har mota suka rakata tana kallan uncle dinta datai missing shima cikin tsananin farin ciki. A motarsa shi da ita ne a baya sai Sayd yana taqi Fiddausi na gaba suka bar zaadens zuwa gida. Suna zuwa masu aiki sukaita mata barka da dawowa Fiddausi ma jin tayi ta samu sukuni ta dawo gida. Palonsa suka wuce ita dashi Fiddausi kuma ta wuce da kayanta duka ta kai mata daki. Firar zamanta a zadeens din taketa basa da yanda kullum suke waya da mama da yanda jan dinta ke tsananin sonta. Sauraronta kawai yake yana kallanta sbd batason tana basa labari yana qin bata hankalinsa shiyasa idan taba basa labari koda wanda baya sone saiya bata hankalinsa ya saurara. Sai datai sututunta ta gaji tafara jin bacci ta tafi daki tai shirin bacci ta kwanta. Shima shirin baccin yayi bayan ya gama waya da mama akan dawowanta gobe tukuna ya kwanta. Washe gari suna gama breakfast ta kira jannah ta fada mata daura 6 days ta dawo gidansu gaba daya. Sai yamma sosai mama suka iso itada Baba alhassan wanda yake nan shima yanxu sbd matansa daya ta rasu tin shekaru biyar yanxu dan haka baida mata yanxu hakama yaransa kowace tana gidan aure daman Sayd ne kawai namiji. Murna sosai su falaq sukai da Fiddausi daga kuma akaita bawa mama labari itama tareda fada mata saura kwana 6 jannah ta taho. Jin hakan mama tai magana da AZIZ din akan inda jannah zata xauna yace zata zauna dakin dayake kusa dana Falaq sai xuwa gaba zaa ware mata bangarenta idan zaayi gyara. Hakan baiwa mama ba amma sbd ya fada dalilinsa saita yadda da hakan tasa aka cire komai na dakin duk da sabbi ne matsu tsananin tsada tasa aka saka mata wasu kayan. Lafiyayyan lefen da aka kashewa kudin gaske da mama ta hada da manyan kudin da sarkokin gwal da English gold din daya kwashe kudade masu yawan gaske mama ta saka su anty maryam da iyalan gidan Alh Ahmed suka kai zaadens wanda ya bawa zaadens mamaki sosai sbd basu dauka AZIZ din zai iya kashe wannan maqudan millions din akan auren da suke tinanin baya so yanxu batareda sun san baimasan da lefen ba shi. Jikin Mimi da jannah sanyi yayi sosai sbd saura kwana uku tafiyan tata, Dad duk yanda yaso magana da AZIZ din yaqi barin su gansa, Sunqi maganar dukiyar aurenta da zasu bada a zuba mata a gidan sbd basason auren ya zama cikakken aure dan haka sukai shiru suma ta wannan bangaren. Anny ce ta dage da shirye shirye sosai tana ragewa jannah damuwar data shiga. Ana gobe tarewan sakonsa ya shigo wayar Dad akan cewa goben by 7 Ammar ya iso da Jannah din limbas. Dad bai taba haduwa da dan adam dayake kallan tsaban idonsaba yayi masa rashin mutunci na kai tsaye ba ba shakkar komai sai LIMBA Amma dai koma menene zai daure ya hadiye sbd yarsa tana hannunsa yanxu tinda aurensa ne akanta. Washe gari kaman ba 'yar datafi kowace mace gata da iko ba a zaadens haka akai shirin tafiyarta. Ammar dayake jin kaman zai mutu ayau din dan zuciyarsa tsananin ciwo take masa hakama kirjinsa kaman zai qone sbd tafasa, Daddy mahmoud ne ya lallaba ya ringa binsa da zantikan da suka sakasa fitowa kaita din da kansa zuciyarsa na neman bugawa. Suna kokarin fitowa Jannah tayi kuka har batada karfi saiga Anty maryam da uwargidan Alh Saad din sunzo da mota biyu lafiyayyu na daukanta mama ta aikosu. Sai alokacin Mimi taji dan sanyi ya dan ratsata sbd ita dai ma bata taba ganin irin wannna kaddararren auren mulkin mallakaba Su kuma su Dad sbd shine kaman yake riqe dasu ya hanasu qarasa zubewa ya sakasu kasa cewa komai wanda ta wani bangaren ba hakan bane su yanxu hanyar da zasu dawo da komai nasu suke nema su nuna masa Jannah tafi karfin duk wani namijin dayake ji da kansa kamarsa dan kuwa akanta zasu iya batar dashi duniyar ma gabaki daya. Su anty maryam ne suka karbo Amarya jannah cikin mutuncin da mutuntawa da girmamawa aka basu ita cikin bada amanar suka tafi da ita tareda Anny da mommy matar daddy mahmoud har Limbas. Baya nan dan haka mama ce ta tarbesu cikeda girmamawa da farin ciki har taiwa Anny da mommy kyautar data dake girgizasu sai guraren 10 suka koma gida. Su Anty maryam ma sunbar gidan guraren 11 aka bar jannah a taredasu mama da falaq da Fiddausi dasuke jin kaman zasu hadiyeta sbd kauna. Karfe goma sha daya da mintina kadan motarsa ta dawo gidan. Sayd ne ya kalli motar Jannah da aka taho da ita aka pake harabar gidan ya juyo kadan ya kalli AY din dake duba sako yace "Ms jannah ta riga ta shigo LIMBAs" Dagowa yayi ya kallesa yace "A goben a kama Dr Abraham din sbd yanxu tana hannuna ko case din batan Dr Abraham ya bayyana zaadens bazasu iya boyeta ba sbd zargin kada akan case dinta su hana asan Gaskiyan tinda batanan" Ajiyar zuciya Sayd yayi sbd finally dai zai fara farautan makasan Ummitah dan kama dr Abraham shine zai bayyanar musu da duk inda Dr ken yake. Parking motar akai suka fito ya nufo ciki kai tsaye yana kashe wayoyinsa sbd hutawa yake buqata a yau daya tabbatarda abinda zaadens sukafi so da kauna a rayuwarsu y shigo hannunsa, Su suna jiran damar da zasu juya rayuwarsa da duk abinda ya mallaka yanda sukaga dama shi kuwa tasa damar akansu har ta shigo hannunsa sai yanda yaga daman juyasu dukansu. #MAMUH ZAFAFA BIYAR KALBIM 500 mamuhgee A DUNIYATA 500 Huguma AJIYA A DUHU 500 Billyn Abdul KIRJIN ME HANKALI 500 Miss xoxo Pay at 0022419171 AccessBank Maryam sani gummi Shedan biya 09033181070 Or mtn vtu at 09032345899*_KALBIM_* _Mamuhgee_ 67 *UMMU_MAHNOOR LUXURIES* (Best luxuries shop) 08034469681 08135142610 Aslm Alaikm ina kuke masu neman luxuries na kayan alfarmar kece raini? Ina masu son su saka sitirar alfarma ta zamani ta manyan mata masu aji da zaa kalleki kallo daya asan sitirar alfarma  e kika saka?   Shin kunsan me ake nufi sa kayan asalin yan gayu da nuna gayu? Sitirar Alfarma kikeson sakawa? Sitirar da kike ganin manyan mata da ita? Sitirarda zakiyi gayun sallah dake da yaranki a dauka waje kikaje da kanki kika siyota? To kizo ga damarki ta sameki sbd UMMU_MAHNOOR LUXURIES ta kawo miki sauki har gida, Karkice se masu kudi ke iya siya har kema me yar dama zaki samu naki da saukin kudi kuma best quality da kalar zamani data yan gayu, Nidai Mamuh nace duk wadda ke son a buga gayun sallan bana da ita da 'yayanta to tazo gurin UMMU_MAHNOOR LUXURIES tai siyayyar sallanta harma zuwa gaba dan nasan zakuji dadi da fahimtar abinda nake fada akan kayanta💯💯 Abubuwan da zaki samu a gurinta with the best quality na wayayyun mata masu aji yan gayu sune; Atampopi Laces Shadda Materials Shoes Bags Veils Trolleys Jewellerys Oil perfumes Numbers 08034469681 08135142610 Handles Instagram @ummu_mahnoor_luxuries TikTok username @ummu_mahnoor_luxuries Facebook ummu_mahnoor_luxuries ******** Bedroom din da aka ware akaiwa gyaran Aljannar duniya akanta su anty maryam suka rakata bayan tin zuwansu suna palon mama suna fira ana sake rarrashinta ganin yanda tai shiru idanuwanta jajir tayi kalan tausayi sosai sbd ta rabu da familynta ba acikin dadin rai ba sbd kaf familyn babu wanda yake cikin farin cikin tarewan tata bayan saleem da Anny wadda ita sbd Son rai take komai. Ammar zuciyarsa bugawa tai a bayan barin jannah mansion din dan haka a cikin daren aka nema likitoci cikin gaggawa dan kaman zai mutu yanayin yaxo masa dan haka gabaki daya hankalin familyn ya tashi suka aje maganar tarewan jannah din gefe suna kokarin ganin an ceto ran Ammar. Falaq ce a dakin nata da Fiddausi dake jera mata kayanta a cikin wardrobe duk da sunada tsananin yawa dan kusan setin akwati biyar ne wanda in total zasuyi kusan akwati 30 babu kuma wanda ba designer set bane kudin akwatinan kadai banda kayan cikinsu zasu ciyar da wasu gidajen na watanni masu yawa. Falaq duk da jan din na cikin damuwa da sanyi sosai kokarin sakawa walwala takeyi amma hakan ya kasa samuwa dan haka ta qyaleta ta zauna kusa da ita tareda riqe hannunta tana kokarin kwantar mata da hankali ta hanyar nuna mata suna tareda ita bata buqatan damuwa tako wane bangare sbd suna tsananin sonta zasu kula da ita kaman a zadeens. Fiddausi kayan lefenta gaba daya da babu abinda aka taba haka ta kaisu closet ta jeresu tareda sauran akwatinan a gefen da aka ware me kyau na jere akwatina kawai. Sake gyara dakin tai ta shiga toilet duk a cikin daren ta jere komai na buqatan jannah din a toilet tareda towels da sukafi guda goma sha biyu ta jere mata su sai rigar wanka bathrobe kusan guda goma itama ta jere ta sake gyara toilet din shima ta fito ta daidaita mata ac ta fice tana kallan time,Karfe goma sha biyu saura. Kitchen taje ta hado ruwa da drink da snacks a tray me shegen kyau da girma ta kawo dakin ta ajiye a table sbd yunwar dare incase ta fice daga dakin tana mata saida safe. Batai wani wankan ba sbd tayi na daren kafin zuwanta nan dan haka kayan jikinta kawai ta sauya sbd suma bazata iya kwana dasu bane ta cire ta saka riga da wando masu kauyi da girma da hula akanta ta kwanta tana rufe idanuwanta tareda sauke numfashi me zafi tana tinanin halinda Dad dinta da Ammar suke ciki sbd sune wainda zasufi kowa shiga damuwar kewanta. Falaq dataso jiran dawowan Daddynta bacci dauketa yayi a palon ba yanda Fiddausi bataiba akan taje daki taqi dan haka dole itama a palon ta tsaya tayata jiran. Lokacinda ya shigo palon akanta idanuwansa suka fara sauka ya kalli Fiddausi datake tsananin jin bacci amma bazata iya yiba sbd tsaron falaq din. Tana ganinsa miqewa tayi ahankali cikeda girmamawa tana masa barka da dawowa. Bai kalletaba Falaq din yake kalla yana ganin farin cikin dayake bayyane a fuskanta duk da tana bacci. Tausayinta yaji ya cike zuciyarsa sbd tana tsananin kaunar macen da zuciyar mahaifiyarta take kirjinta batareda tasan bugun zuciyar mamanta ne take jiba wanda kila hakan ne ya sakata tsananin so da kaunar Jannah din haka sosai, A rayuwarta shi kadaine wanda sonsa yafi mata komai na duniya sai yanxu dayake ganin tanawa jannah wannan son wanda yake sakata farin ciki da walwala sosai. Qarasawa yayi gurinta ya durqusa ahankali ya shafa fuskanta ahankali kafin ya dauketa gaba dayanta ya nufi dakinta Fiddausi na biye dashi, Sayd kuwa juyawa yayi ya nufi hanyar palonsa da bedroom dinsa yana kashe wayoyinsa duk da yakamata yayi aiki yau da dare amma zai bari zuwa da safe. Kwantar da ita yayi ya rufeta yana mata addua a natse yana gamawa ya sake gyara mata rufa ya rage mata ac. Fiddausi ce ta kashe komai suka fice daga dakin ya wuce ta kofar dakin da jannah take ciki kwance idanuwanta rufe damuwa da sanyin jiki cike fal da kirjinta. Fiddausi ma dakinta ta wuce tanajin gajiya sosai ta sauya kayanta zuwa na bacci ta goge fuskanta da wipes ta kwanta tana addua take bacci ya dauketa sbd a tsananin gajiye take. Washe gari tinda falaq ta gama asuba take son zuwa dakin jannah amma tana fasawa sbd tina fadan mama dataita maimaita mata karta ringa zuwar mata da asuba koda daddare sosai sbd kada ta takura musu itada Daddynta. Har gari ya fara haske tana son zuwa amma jin ba motsin kowa dole ta koma gadonta ta kwanta ta koma bacci. Jannah dayake bata samu baccin daren ba saida tai sallar asuba baccin yazo mata bayan tayi waya da Mimi da Dad dinta yace mata komai lafiya tukuna ta kwanta bacci me karfi ya dauketa. Dayake kowa hutu yakeson samu a gidan sbd yar hayaniyar da akai jiyan ta tarewan baquwansu shiyasa babu wanda ya fito da wuri tsit sai masu aiki dake kaida kawon aikinsu cikin rashin hayaniya suka gyare koina fes koina sai kamshin luxuries yake da Sanyin Ac ba hayaniya. Ita kanta Fiddausi bata fito da wuri ba sbd ita kaman ta zama family duk da mai aikince amma aikinta na musamman ne kuma duka masu aikin gidan a karkashinta suke dan haka bata fitoba sai kusan karfe goma tana isa kitchen aikin breakfast din mutan gidan ta fara cikin tsari da yanda tasan kowa na son komai nasa ya kasance. Tana gamawa tafara jere komai a dining din sai alokacin suka fara fitowa. Mama ce tafara fitowa tana waya cikin riga da zani na wani lallausan lace mara nauyi da hayaniya sai tsada kunnuwanta kuwa daman gwal ne a jikinsu tintini tasaka normal gwal ta saka English duk wanda taga dama sakwa takeyi sbd bata son masu nauyi dan haka idan kagani ma bazaka dauka gwal bane sbd yanda suke simple da rashin ado sosai. Zaunawa take kokarin yi falaq ta fito daga dakin jannah tareda jannah din datake sanye da Riga da skirt na lace mara nauyi ko kadan itama se tsada navy blue kala daya kwanta a jikinta ya fidda lafiyayyan shape dinta. Qaramar veil ce akanta wanda iya kacinta wuyanta dan bata iya saka babbar gyaleba batama taba sakasa ba rayuwarta dan haka qaramar veil din data tsaya wuyanta duka sauran jikinta a bayyane yake duk da bawai kamata kayanta yayiba amma daidai jikinta ne. Falaq ma dakinta ta koma ta sauyo kayanta zuwa irin na jannah din sbd kusan duka kayansu sunada iri dayane sbd duk abinda zata dinka guda biyu take dinka musu itada falaq sbd falaq na son kayan hausa sosai tinda bata taso tana sakasu ba shiyasa take kaunarsu sosai. Gurin mama jannah din ta qaraso cikin nutsuwa da girmamawa ta gaidata tana dan kokarin korar da damuwan datake fuskanta wadda ta kwana a cikinta. Cikeda kauna da kulawa batareda damuwa da qaramin mayafin dayake wuyan jannah dinba mama ta miqa hannu ta kama na jannah din ta zaunar da ita gefenta tana amsawa da cewa "Jannah yaya baqunta? Karki saka damuwa sosai a ranki nan din gidanki ne, Kece matar gida ki sakewanki zakiji dadi zama damu sosai sbd muna muna kaunarki kamansu Mimi, Banason ki takura kanki ko kadan kinji, Shi kansa AZIZ din rayuwa dashi itace best rayuwar da zakiyi alfahari da ita, Badan ina mahaifiyarsa ba nake yabansa tabbas Zakiji dadin rayuwar aurenki a Limbas, Allah yayi muku albarka ya sakawa aurenku albarka da kwanciyar hankali har tsufa da jikoki insha Allah kuna tare." Amin" falaq take cewa tana qarasowa gurin kafin ta zauna ta juya tayi hanyar palon Daddynta. Sake juyowa tayi zatai magana Mama tace "Zo ku tafi da Jannah ku gaida Bestyn naku tinda kince yanzu keda ita kuke dashi,ni danake uwarsa na tashi a banza kenan bana cikin lissafi" Dawowa tayi da sauri tana kama hannun jannah din wadda gabanta ya fadi jin abinda mama ta fada ta dago fararen idanuwanta ta kalli hannun falaq dayake kama nata ta kasa kallan mama datake jin kunyar tace mata aa batason zuwa. Fiddausi kuwa dariya tayi tana cewa "Mama ke ai tini 'yarsa ta rabaki da naki dan tinda tintini tace ita kadai take dashi sai yanzu da akai arziki ta yadda itada Anty Jannah take dashi" Cikin sakewa mama tace "Iyi ai kibar yar Albarkar yarinya dan bazance jaira ba duk ta gama zama jairar dan haka gwara mu koma cewa yar albarka din tayita samun albarkar" Kallan jannah data kasa motsawa maman tai tana cewa "Kuje ku gaidasa kun fito tare cin abinci" Rikitaccen numfashi ta sauke a boye me zafi tana miqewa kafafunta na sanyi falaq na sake riqeta suka nufi inda falaq din ke dosa dasu bugun zuciyarta na tsananta. Suna barin gurin mama tabi bayanta da kallo tana jin kaunarta ta sake shigarta Allah ya cika mata burinta na shekaru yau ta wayi gari a gida daya da matar AZIZ saura jikokinta suma tana fatan Allah ya nuna mata ta wayi gari hayaniyarsu ta cika mata gidan. Sanyi jikinta yayi sbd Allah beyi fatima ce zata ga hakan ba itace take ganar mata duk da kaman yanda AZIZ bai cire rai daga mahaifiyarsa ba koyaushe bincikensa akan inda take bai taba tsayawaba tinda ya tsayu da kafafunsa yana fatan wata rana ace an samo masa inda take itama hakane bata taba cire rai da sake ganin fatima wadda suke fatan duk inda take ta kasance tana cikin Aminci da kariyar ubangiji. #MAMUH ZAFAFA BIYAR KALBIM 500 mamuhgee A DUNIYATA 500 Huguma AJIYA A DUHU 500 Billyn Abdul KIRJIN ME HANKALI 500 Miss xoxo Pay at 0022419171 AccessBank Maryam sani gummi Shedan biya 09033181070 Or mtn vtu at 09032345899*_KALBIM_* _Mamuhgee_ 68 *UMMU_MAHNOOR LUXURIES* (Best luxuries shop) 08034469681 08135142610 Aslm Alaikm ina kuke masu neman luxuries na kayan alfarmar kece raini? Ina masu son su saka sitirar alfarma ta zamani ta manyan mata masu aji da zaa kalleki kallo daya asan sitirar alfarma e kika saka? Shin kunsan me ake nufi sa kayan asalin yan gayu da nuna gayu? Sitirar Alfarma kikeson sakawa? Sitirar da kike ganin manyan mata da ita? Sitirarda zakiyi gayun sallah dake da yaranki a dauka waje kikaje da kanki kika siyota? To kizo ga damarki ta sameki sbd UMMU_MAHNOOR LUXURIES ta kawo miki sauki har gida, Karkice se masu kudi ke iya siya har kema me yar dama zaki samu naki da saukin kudi kuma best quality da kalar zamani data yan gayu, Nidai Mamuh nace duk wadda ke son a buga gayun sallan bana da ita da 'yayanta to tazo gurin UMMU_MAHNOOR LUXURIES tai siyayyar sallanta harma zuwa gaba dan nasan zakuji dadi da fahimtar abinda nake fada akan kayanta💯💯 Abubuwan da zaki samu a gurinta with the best quality na wayayyun mata masu aji yan gayu sune; Atampopi Laces Shadda Materials Shoes Bags Veils Trolleys Jewellerys Oil perfumes Numbers 08034469681 08135142610 Handles Instagram @ummu_mahnoor_luxuries TikTok username @ummu_mahnoor_luxuries Facebook ummu_mahnoor_luxuries ****************** Duk taku daya da suke qarawa na zuwa palon nasa tsananta bugun zuciyarta yake dan haka kafafunta suka qara sanyi kaman bazata iya qarasawa ba takeji sedai kuka mama na palo tana jiran zuwan nasu hakama falaq na maqale da hannunta tana jin kaman suyi gudu su isa da wuri. Rikitaccen numfashi me zafi mara sauti ko kadan ta sauke a lokacinda falaq ta bude kofar palon kai tsaye wani irin sanyi dayake cikeda qamshinsa tako ina ya bigo a fuskanta yana shiga hancinta tareda qarasa yamutsa bugun zuciyarta gabaki daya. Bude idanuwanta tayi ahankali cikin nutsuwa tana kallan cikin palon da babu kowa ta sake sauke boyayyar ajiyan zuciyan farin cikin baya nan. Zaunar da ita falaq tai tana juyawa da sauri zata tinkari bedroom dinsa jannah din tai saurin riqe hannunta tana kallanta sbd ta fahimci ina zata ta bude baki a natse tace "Ina zakije? "Zanje na dubosa ne a bedroom dinsa" Sake kallanta jannah din tai dakyau tana mamakin rashin wayonta sam, A hakan yake iya bude baki yace tarbiyan gidansa tafi ta wasu. Dawo da falaq din tai gefenta ta zaunar cikin nutsuwa ta kalleta tace "Bakisan kinyi girman da bai kamata kina shiga dakin Daddynki kai tsaye ba? Kin girma kin zama yan mata ke kina buqatan privacy a daidai wannan shekarun naki dan haka shima daddyn yana buqatan privacy...." Katseta falaq tai da cewa "Ai babu me shiga duniya idan bani ba ni kadaice nake shiga bedroom dinsa nima sbd ina yarsa ne" Girgiza mata kai jannah tai tana kama hannunta cikin kulawa tace "No kema kinyi girman daya kamata ki dena shiga kwata kwata idan ba shine ya kira ba, Ba daddynki kadai ba bedroom din kowane namiji a duniya karki sake shiga saina mijinki kadai idan anmiki aure, Baa shiga Addininmu ya hana hakan kwata kwata baayi ki kiyaye sosai karki sake saina mijinki,kinji??? Shiru falaq tai tana nazarin zancenta sbd Daddynta daman yana fada mata kowane namiji a duniya karta yadda ko hannunta ya kama koda da sunan gaisuwa, Yasha fada mata hakan tin tana yarinya sosai haryanxu bai dena fada mata shiyasa iya shi kadaine take iya hada jikinta da nasa sbd shi mahaifinta ne batama iya zama idan baa kusa dashiba ta maqalqalesa indai yana kusa. Kallan jannah tai cikin dan tinanin daya rikitar mata da tinani tace "Kikace harda dakin Daddyna na dena shiga sai nayi aure? To idan nayi aure saina ringa shiga dakin Daddyn kome?? Shafa fuskanta tayi tace "No idan kinyi aure dakin mijinki kawai zaki ringa shiga banda na daddynki, Kwata kwata dakin kowane namijin daga yanxu kin dena shiga saina mijinki har tsufa, Idan kika shiga dakin wani zai iya cutatar dake kaman irin yanda kika ringa jin tsoro a school lokacin" Kallanta falaq tai da sauri tana fahimtar abinda take nufi dan haka ta sauke ajiyan zuciya tana gane abinda yasaka kenan Daddynta yana rufe bedroom dinsa wasu lokutan da safe saitayita bugawa yazo ya bude mata. Kallan jannah ta sakeyi tace "To ke zaki iya shiga kenan tinda ke mijinkine nima idan nayi aure nima ni kadai zan shiga na nawa mijin ko?? Faduwa gaban Jannah yayi ta kalli falaq din da sauri tace "Aa ni yanzu nima bazan iya shigaba sai matarsa" "To ai kece matarsa Jan" Mantawa jannah tai da fada hakan sbd rikicewan datai ta sake kallan falaq tace "Yanxu bai tashiba inaga and ba buqatan tadashi mu tafi kawai idan ya tashi ya fito saimu gaidasa acan." Sam falaq bata yadda da hakanba sbd bata taba zuwa ta fita ziqau batareda taga daddynta ba dan haka miqewa tai tana kama hannun jannah din tana ja zuwa hanyar master bedroom dinsa tana cewa "To muje tare da matarsa da yarsa tinda ni kince na dena shiga ni daya" Da sauri jannah take kokarin janye hannunta zata juya aka bude kofar Bedroom din wanda ya sakasu tsayawa cak dukansu itada falaq din suna kallan kofar. Qamshinsa da koina yakeyi tin daga palon har koina ne ya bugo mata daga cikin kofar datake buden ta dago idanuwanta masu kyau ta kallesa. Sanye yake da Ash balmains na wata crazy shirt me shegiyar tsada da straight wando sai tsadaddun shoes din dake kafarsa na ballies. Fuskansa wani irin sabon sirrin kyau ne na safe wanda idan ka fito kafin ka fara hayaniya ko fita a cikin haske kake kasancewa fresh dinka wasu na kiran hakan da morning beauty ko morning freshness. Fin karfinta zuciyarta tai ta kasa dauke fararen idanuwanta akansa tana masa wani irin kallan dayake bayyanarda gabaki daya sirrin dayake boye a zuciyarta, Tsananin azabtuwan da zuciyarta take akan tsananin sonsa dayake maqale a cikinta ne idanuwanta ke loosing control gurin bayyanawa har idanuwan na cikowa da hawayen da batasan dasuba. Falaq tsayawa tayi kallanta cikeda tausayawa sbd duk da ba komai take ganewa ba tasan Jannah na tsananin son Daddynta hakama a yanxu din kallo ne na ganin abinda zuciya take tsananin so amma ta kasa samu. Ahankali ya qaro taku biyu ya tsaya a gabanta ya dan rankwafo kadan batareda ya kalli cikin idanuwanta ba ya kai bakinsa gefen fuskanta daga nesa kadan sbd kada falaq taji abinda zai fada da wata muryan data sakata qanqame hannuwanta a jikinta sbd kauri da tsananin nutsuwa da taushin muryan yace "Me kikeson koyawa yarinyana? Learn to control your feelings Ms, Sbd kada ko koyar da ita irin hakan bata isa sanin kallan meye wannan ba" Skipping bugawa zuciyar Jannah tai sbd tsananin kunya da baqin cikin maganarsa tareda wani irin qamshin dataji yana shiga hancinta wanda ta tabbatarda daga bakinsa yake fitowa kaman na lemon da mint sun hadu. Dagowa yayi yai mata kallo daya yaga yanda idanuwanta ke cikowa da hawayen kunya da baqin ciki yayi gaba yana amsa maganar falaq a natse. Rawa jannah taji kaman kafafuwanta sunayi kasa riqe hawayenta tai saida suka sauko ta saka hannunta ta share tana juyowa da kyar ta biyu bayansu. Mama na ganin fitowansu taji farin ciki ya sake cikata cikin farin cikin ganinsu tace "Falaq meyasa ke wai bazaki girma bane kinbi kin kanainayesa bazaki bari itama jannah din ta samu damartaba." Gaida maman yayi yana hanasu cigaba da zancen ta hanyar janyowa mama wani zancen daya san zai dauke hankalinta gaba daya. Dining suka nufa banda jannah dataji ta kasa sakewa kwata kwata hakama taqi yadda ta sake kallansa sbd kada ya kuma tozartata. Mama ce ta jata da kanta har Dining din ta zauna a kusa da maman saiga Sayd shima yazo ya zauna yana gaida mama itama kallanta yayi da kulawa suka gaisa kafin ya maida hankalinsa kan falaq datake gaidasa tanason basa labarai amma ba dama dole sai angama. Suna fara breakfast din babu wanda ya sake magana hakama ita dai bata dagoba ta kallesa. A natse taci Fried potatoes da liver sauce sai ketchup da kuma tea mara zafi sbd bata wani son zafi sosai a abinci. Shi kansa abinda yaci kenan sai falaq da sayd da sukaci Da kwai da plantain mama kuwa kunin gyada ta hada dashi wanda yaji madara sosai yayi kauri da haske sosai. Jannah dince ta fara gamawa amma bata bar table din ba sbd girmama su maman. Shine ya fara miqewa yabar dining din sayd yabi bayansa sai a lokacin falaq ta dawo gurinta. Saida mama ta gama tabar dining din itama ta miqe tareda falaq suna kokarin barin dining din Fiddausi tazo tafara tattara gurin. Bedroom dinta ta koma ta zauna tana janyo wayarta ta sake saka kiran Dad dinta wanda basuyi magana ba da safen. Waya ta fara yi da familynta da suka boye mata halinda Ammar yake ciki ta debewa kanta kewa sosai da wayan. Lokacin sallah nayi tayi sallah ta sauya kayanta zuwa marasa nauyi sosau sbd ta saba bata iya wuni da kaya masu nauyi a jikinta. Fitowa tai ta nufi kitchen dan taya Fiddausi aiki sbd zaman shirun ya isheta. Falaq ma binsu tai kitchen din duka masu aiki suka fice daga kitchen din aka barsu sbd girmamawa. Abincin rana din suka kammala a tare Fiddausi ta jera a dining ita kuma ta nufi dakinta ta sake wanka tanajin yar gajiya ta kwanta dan ta dan huta. Sai yamma sosai ta fito lokacin su mama already sunci abincinsu dan haka ita kadai ta nufi dining din ta zauna falaq na islamiyya. Gidan tsit ba hayaniya sbd Fiddausi na kitchen mama kuma tana can palonta. Abincin ta zuba brown spaghetti ce dataji kidney da liver dasu vegetables sai kazan da aka gasa da vegetables. Daidai cikinta ta zuba abincin ta zuba orange juice a cup tana fara ci kenan Fiddausi tazo dining din ta saks jera wasu abincin tana barin gurin qamshinsa ya doso gurin ta dago ahankali ta kalli hanyar shigowa dining room din daidai yana sako kai sanye da kayan shan iska alaman ya dade da dawowa daga aiki haryayi wanka. Fararen qafafunsa da gashi me kyau ya kwantawa taiwa kallo daya ta juyo da kanta sbd three quarter Fendis ne a jikinsa farare da suka maidasa wani lafiyayyan Kyakkyawan matashi me ji da hutu da aji. Shi kansa baiyi tinanin ganinta a dining dinba a daidai wannan lokacin dan haka ko kallanta bai sake yiba saida ya zauna ya kalleta itama shi ta dan dago zata kalla ta gaida zancensa ya katsata da cewa "Akwai dabiun na rashin tarbiya da kikaxo dasu da kike buqatan sauyawa sbd tarbiyan tawa yar, Na koyawa yata girmamawa da gaida na gabanta gashi ke da alama baki samu hakan ba" Qarasawa yayi yana bayyanarda takaicinsa da mamakin rashin hankali da tinani irin na zaadens da babu abinda suka iya sai son zuciya da haryanzu suke a cikinsa. Dagowa tayi idanuwanta na sauyawa sosai da tsananin ciwon zancensa ta bude baki jiki a mace zata gaidasa din ya daga mata hannu yana nuna mata abincin dayake kan table din da hannu fiskansa a daure sosai baya ko kaunar kallanta a gabansa. Dan sunkuyar da kanta tayi ta hadiye hawayen da suka ciko idanuwanta ta miqe ta zagaya gefensa tafara serving dinsa hannuwanta na dan rawa zuciyarta cikeda damuwan datakejin kuka da kewan gidansu na zuwar mata. Dauke kallansa yayi daga hannuwanta dake rawa yana cewa abincin ya ishesa. Ruwa da juice din da Fiddausi ta shigo dashine taga yanda jannah din hannuwanta ke rawa ta qaraso ta ajiye ta juya. Ajiye masa komai gabansa jannah din tai ta koma ta zauna sedai ta kasa cigaba da cin abincinta daci zuciyarta ke mata dan haka miqewa tayi ahankali tabar gurin jikinta a mace. #MAMUH ZAFAFA BIYAR KALBIM 500 mamuhgee A DUNIYATA 500 Huguma AJIYA A DUHU 500 Billyn Abdul KIRJIN ME HANKALI 500 Miss xoxo Pay at 0022419171 AccessBank Maryam sani gummi Shedan biya 09033181070 Or mtn vtu at 09032345899*_KALBIM_* _Mamuhgee_ 69 *UMMU_MAHNOOR LUXURIES* (Best luxuries shop) 08034469681 08135142610 Aslm Alaikm ina kuke masu neman luxuries na kayan alfarmar kece raini? Ina masu son su saka sitirar alfarma ta zamani ta manyan mata masu aji da zaa kalleki kallo daya asan sitirar alfarma e kika saka? Shin kunsan me ake nufi sa kayan asalin yan gayu da nuna gayu? Sitirar Alfarma kikeson sakawa? Sitirar da kike ganin manyan mata da ita? Sitirarda zakiyi gayun sallah dake da yaranki a dauka waje kikaje da kanki kika siyota? To kizo ga damarki ta sameki sbd UMMU_MAHNOOR LUXURIES ta kawo miki sauki har gida, Karkice se masu kudi ke iya siya har kema me yar dama zaki samu naki da saukin kudi kuma best quality da kalar zamani data yan gayu, Nidai Mamuh nace duk wadda ke son a buga gayun sallan bana da ita da 'yayanta to tazo gurin UMMU_MAHNOOR LUXURIES tai siyayyar sallanta harma zuwa gaba dan nasan zakuji dadi da fahimtar abinda nake fada akan kayanta💯💯 Abubuwan da zaki samu a gurinta with the best quality na wayayyun mata masu aji yan gayu sune; Atampopi Laces Shadda Materials Shoes Bags Veils Trolleys Jewellerys Oil perfumes Numbers 08034469681 08135142610 Handles Instagram @ummu_mahnoor_luxuries TikTok username @ummu_mahnoor_luxuries Facebook ummu_mahnoor_luxuries *********** Shima ruwa ya dauka yasha a natse ya miqe yabar gurin batareda ya qarasa cin abincin ba. Fiddausi dataga yanayin da jannah ta wuce a cikinsa dakinta ta bita ta zauna tana tayata fira tana sake gyara mata dakin tin tana kasa cewa komai har ta biyewa Fiddausi din suna fira tana bata labarin kuruciyan falaq da yanda suke fama da ita a lokacin idan daddynta yayi tafiya ta gane bayanan. Dadin firar jannah takeji sosai zuciyarta na sanyi da jin yanda falaq ta taso wanda a cikin firar ta fahimci kila a gurin haihuwan falaq mamanta ta rasa ranta sbd a kaf labarin babu inda aka fadi asalin mamanta,Fiddausin ce kenan ta reneta tin tana jaririyarta itada mama dan haka kauna da jin falaq din a zuciyarta ya qaru taji zata iya daure komai sbd bawa falaq din kauna irin ta uwa data rasa duk da tariga tasan har abada babu me iya hawa matsayin da mahaifinta ya riga ya cike na uba dana uwa dan kuwa koda uwartata zata dawo duniya to bazata iya cike gurbin daya riga yacikeba sedai kwatantawa sbd ita kanta falaq din babu wani dan adam dayake duniya da zata iya bawa matsayin data bawa mahaifinta ba sbd ba qaramin tsananin kauna take masa ba dan duk da tana yarinya babu abinda takejin bazata iyaba sbd daddynta shiyasa taiwa Ammar tsanar gaske duk da bata gama sanin tsanar me take masa dinba. Har magrib Fiddausi na dakinta tana tayata fira da kalle kallen da suke a ipad ga kuma qatuwar flat screen tv datake dakin nata dayakeda girma sosai. Falaq na dawowa kai tsaye dakin ta nufa tana ganinsu ko uniform na islamiyya din bata cireba ta xauna cikinsu jannah na tayata cire hijab din jikinta dayake qamshi me dadi duk da anyo yawon makaranta amma sbd tsadan turarenta da ake siya mata yasaka komai na jikinta qamshin yakeyi me sanyi. Hularta ta jannah ta zame mata sbd tasha iska tana cewa "Falaq kodai zaki cire uniform din kiji dadi?" Girgiza kai tayi tana shan ruwan da Fiddausi ta miqa mata cikeda kulawa. Mama data jisu shiru ta dauka basa nan sai bayan magrib suka fito dukansu kowannensu da walwala akan fuskansa. Kallan falaq tai da uniform a jikinta tace "Me kikeyi da uniform a jikinki har yanzu falaq? Oh ni Sakina wannan yarinya anyi shiryayya" Murmushi jannah tai tana cewa "Ko data dawo mama ta gaji ne shine ta huta sai yanzu zata sauya" Kallan jannah mama tai tana cewa "Allah na gode maka,kema yanzu jannah sahun AZIZ zaki bi kuna biye mata komai tayi bata laifi daidai ne ko?? Murmushi jannah din ta sake yi tana kallan falaq tace "Je ki kicire uniform din kilama sunata damunki" Dariya mama tayi tana kallan Fiddausi kaunar jannah na sake cikata tace "To ai shikenan saiku bada himmar qarasa lalatata kunyiwa mijinta bayani daga baya" Falaq na jin hakan ta dawo da sauri tana cewa "Mama Jan tace na dena shiga dakin Daddy tinda safe ba kyau sai nayi aure dakin mijina kawai zan ringa shiga karna sake shiga na kowane namiji sai nasa" Mama cikeda mamakin falaq din tace "To wannan nasihar datai miki wayace miki ana fada?baa fadawa kowa gaskia ta fada miki" Basusan da isowansa ba sai zancensa sukaji wanda ya sakasu yin tsit Fiddausi na hadiye hadiyarta da sauri tana kama kanta. "Wane mara hankalin ne ya sakata fadawa yarinya hakan? Fuskansa a daure take sosai bacin ransa na bayyana a cikin sautinsa dayake fita a natse ya kalli jannah din wadda ta kasa dagowa Yace "Wane kalan tarbiya ne kikazo dashi? So nawa zan fada miki tarbiyanku dana mutane ba daya bane, Kinsan inda maganganunki zasu kai tinaninta? Meya hadata da maganar zuwa dakin miji a wannan shekarun? Ke tin kina yarinya qarama aka nuna miki xuwa dakin mijin ne or wat?? Like seriously?? Mama ce ta katsesa da cewa "AZIZ me kake fada haka? Tana bata tinani me kyau ne ai sbd tintini ya kamata ta dena shiga dakinka anyhow, Ta girma ya kamata tafara sanin ta girma hakama tin a yanzu ne ya kamata tasan baa shiga dakin kowane namiji saina mijinta idan akai mata aure shima" Hawayen da jannah ta kasa barin su saukone ta hadiye su ta maqoshinta suka wuce mata da wani irin daci ta kasa dagowa. Shi kuwa maman ya kalla yace "Mama duka wannan zancen ba yanxu ne lokacin yinsu ba, Tana buqatan kiyaye kalan namu tarbiyan da dabiun dasu basuda shi banason zance kowane iri yana shiga kunnen Falaq din" Falaq jannah din ta zubawa ido itama nata idanuwan na cikowa da hawaye ta miqe ta koma gurinta tana rungumeta ta dago ta kalli daddyn nata tana bata fuska. Mama ma tausayin Jannah din taji duk ya rufeta amma bata ji zafin AZIZ din sosaiba sbd ganin take bai saba da kowa na saka masa hannu ko baki bane a tarbiyan yarsa bayan ita da sayd dasu kadai ne suke masa discipline nata. Fiddausi silalewa tai tabar palon jiki a mace Sayd ma dayake tare dashi shiru yayi sbd ba hurumin shigar kowa bane bayan maman sai kuma falaq da itama take iya sakasa da hanasa. Cikin karfin hali jannah ta dago tana hadiye damuwa da radadin zuciyanta tana nunawa mama ba komai bayan barinsa gurin. Falaq zuwa tai ta cire uniform dinta taqi sake fitowa dakinta har lokacin cin abinci yayi taqi fitowa karshema rufe dakinta tayi. Tin Fiddausi na daukan abin wasa har taga dai da gaske take take hadda su kuka sosai dan haka ta fito ta sanarwa su jannah da mama. Jannah ce ta nufi dakin ta ringa Knocking tana kiran sunanta cikin kulawa da rarrashi. Qin budewa tai wanda hankalinsu ya fara tashi sbd kuka takeyi sosai taqi magana. Jannah hankalinta mugun tashi yayi sbd tana gudun AZIZ din yaji ta sake wani laifin dan haka ta ringa rokon falaq din akan ta bude amma sam taqi. Mama tasan zaayi hakan daman Falaq din na wannan sakarcin har sai Daddyn yamata abinda takeso idan ba hakan ba haka zata qi fitowa ta dagawa kowa hankali. Basu san abinda yake faruwa ba sai da ya dawo kusan 10 na dare ya tararda Fiddausi da jannah din tsuru cikin damuwa. Ko kallan inda suke baiyiba ya wuce hanyarsa yana duba time. Sayd ne ya kalli Fiddausi yace "Lafiya dai?akwai abinda yake faruwa ne? Hanyar da AY yabi Fiddausi ta saci kalla tace "Falaq ce tin bayan magrib tana daki ta rufe tanata kuka sosai kuma tin dazu ma munji shir.......... Cak din da AZIZ din ya tsaya cak sbd maganarta tsaf a kunnensa ta saka ya saka Fiddausi kasa qarasawa tana sauke kanta qasa. Shi kansa Sayd din da sauri ya juya ya kalla ko AZIZ din ya shige ya gansa yana sauya hanya zuwa bedroom din Falaq wanda jannah ke can tsaye tin dazu idanuwanta duk sunyi ciki ita kanta tana cikin tsananin buqatan me kulawan da ita tai kalan tausayi jikin yayi tsananin sanyi sbd tasan itace zata hadiyi baqin cikin akan wannan lamarin. Jin qamshinsa da taku a bayanta ya sakata janyewa gefe tana juyowa taga shi dinne kuwa fuskansa babu sauki ko kadan. Tsayuwa yayi a bakin kofar ya ambaci sunan falaq da muryansa kai tsaye. Kafin ya sake kiran falaq din juyowa yayi cikin zafi ya kalli jannah din ransa na quna yace "Babu abinda kika daidai ne a rayuwanki ke?? Idan ta rufe kanta kusan awa biyar me amfaninki da bazaku nema mutane ku fada musuba? Cikin tsananin sanyi da mutuwan jikinta datake jin zazzabi sbd wahalar tsayuwa da buga kofa ta bude baki a sanyaye tace "I'm sorry" Kaman tafasashen ruwa haka yaji muryanta datake bayyanarda itama ciwone a jikinta na sauka a zuciyarsa, Da karfin gaske ya buga kofan yai wa falaq din kira daya daya saka falaq din mugun firgita sbd bata taba jinsa hakan ba. Ita kanta Jannah sarawa kanta yayi sbd faduwan gaba ta dafa bango. Acan ciki kuwa falaq ciwonta ne ma ya tashi jin tai kaman numfashi na gagara shiga cikinta, Bugun zuciyarta tsananta yayi sosai har tana jin azabarsa ta dafe kirjinta tana jin abinda bata taba jiba. Saukowa tai daga gadonta bata gani sosai jiri na dibanta tana son isa kofar sedai ko taku uku bataiba ta zube a tsakiyar dakin. Jin faduwanta a qasa ya sakasa juyawa da sauri yace Sayd ya kawo keys. Da gaggawa aka kawo keys ya bude dakin Ganinta zube qasa ya sakasa jin kansa gabaki daya ya dauki zafi da saurin gaske ya isa gareta ya dauketa cak yana sayd yayi sauri ya kira likita. Jannah ma tashi hankalinta yayi taji gaba daya ta rasa kuzarin jikinta ta rabe gefe tana kallan yanda falaq komai nata baya motsi. Sayd da sauri ya fidda wayarsa yana ficewa daga dakin ya saka kiran sabuwan dr din da suka samu anan din mace da namiji ta bangaren ciwon falaq kawai. Ganin ya rasa taimakon da zai bawa falaq din ya saka jannah zuwa bakin gadon tafara taimaka mata ganin numfashinta bai tsaya gaba dayaba sbd tayi karatun bada taimakon gaggawa a Greece sbd yanayin ciwonta hakama Ammar ya koyar da ita abubuwa da dama sbd koda wani abin zai sameta ba kowa dan basa wasa da lafiyanta sam. Yanda takeyiwa falaq dinne cikin taka tsantsan da kulawa ya sakasa kallanta yana jiran jin wani abu daga gareta sbd ganin falaq din tana dan kokarin daidaituwa a yanda kirjinta ke wani irin ja. Baa dauki lokaci irin sosai dinnanba dr Sameera ta iso tareda wata nurce. A lokacin mama data shige tini ta fito duk suna palo cikin damuwa Fiddausi idanuwanta sunyi jajir sbd Kauna ce me karfi da shakuwa kamar uwa da 'ya itama a tsakaninta da falaq sbd shayar da ita ne kadai bataiba amma duk wata dawainiyar falaq itace meyi tin falaq na zanin jariranta. Jannah ma a zaune take sanyaye zazzabi me karfi ne itama yake cinta na walaha. A gidan dr Sameera ta kwana Sai Falaq ta farka. Dr Sameera kwararriya akan aikinga kuma mace ce Kyakkyawa mai kyan jiki da tsari tareda ilimi sosai kuma tin ganin farko Allah itama ya jarabceta da kaunar AZIZ LIMBA wanda bai taba mata kallo biyu xuwa uku ba ko yau din datake cikin gidansa sbd 'yarsa. A dakin Falaq dr Sameera ta kwana ya hana jannah kusantarta kwata kwata wadda ta kwana cikin damuwa da zazzabin da batada maganinsa. #MAMUH ZAFAFA BIYAR KALBIM 500 mamuhgee A DUNIYATA 500 Huguma AJIYA A DUHU 500 Billyn Abdul KIRJIN ME HANKALI 500 Miss xoxo Pay at 0022419171 AccessBank Maryam sani gummi Shedan biya 09033181070 Or mtn vtu at 09032345899*_KALBIM_* _Mamuhgee_ 70 *UMMU_MAHNOOR LUXURIES* (Best luxuries shop) 08034469681 08135142610 Aslm Alaikm ina kuke masu neman luxuries na kayan alfarmar kece raini? Ina masu son su saka sitirar alfarma ta zamani ta manyan mata masu aji da zaa kalleki kallo daya asan sitirar alfarma e kika saka? Shin kunsan me ake nufi sa kayan asalin yan gayu da nuna gayu? Sitirar Alfarma kikeson sakawa? Sitirar da kike ganin manyan mata da ita? Sitirarda zakiyi gayun sallah dake da yaranki a dauka waje kikaje da kanki kika siyota? To kizo ga damarki ta sameki sbd UMMU_MAHNOOR LUXURIES ta kawo miki sauki har gida, Karkice se masu kudi ke iya siya har kema me yar dama zaki samu naki da saukin kudi kuma best quality da kalar zamani data yan gayu, Nidai Mamuh nace duk wadda ke son a buga gayun sallan bana da ita da 'yayanta to tazo gurin UMMU_MAHNOOR LUXURIES tai siyayyar sallanta harma zuwa gaba dan nasan zakuji dadi da fahimtar abinda nake fada akan kayanta💯💯 Abubuwan da zaki samu a gurinta with the best quality na wayayyun mata masu aji yan gayu sune; Atampopi Laces Shadda Materials Shoes Bags Veils Trolleys Jewellerys Oil perfumes Numbers 08034469681 08135142610 Handles Instagram @ummu_mahnoor_luxuries TikTok username @ummu_mahnoor_luxuries Facebook ummu_mahnoor_luxuries ***************** Washe gari tinda safe Jannah ta nufi dakin Falaq kafin ya fito ta dubata bayan sun gaisa da dr Sameera wadda ke bin jannah din da kallo sbd sanin itace matar AZIZ LIMBA din. Ta jima a dakin bayan ta dan tambayi dr Sameera din yanayin jikin falaq din ta bata tabbacin zata iya farkawa kowane lokaci. Kasa komawa dakinta tai ta nufi dakin mama tai mata ina kwana mama ta sakata tai zamanta anan tai baccin safenta wanda bata samu tayiba da dare sbd cikin tsananin zazzabi da yunwa ta kwana. Karfe goma da mintina ta farka ta sake zuwa dakin Falaq ta dubata kafin ta wuce dakinta tai wanka ta shirya ta fito tana waya da Maheer kafin ta kashe tana isa dakin falaq ta tarar da tana farkawa dan haka da sauri ta qarasa gareta tana zaunawa gefenta shima a daidai lokacin ya shigo a karo na babu adadi. Falaq na ganinsa idanuwanta suka ciko da hawaye suna gangarowa.. Jannah ta zari tissue tana share mata hawayenta cikesa kulawa da kauna. Dr Sameera ficewa tai a dakin aka barsu su kadai. Miqewa jannah tai ta basa guri zata bar dakin Falaq ta kalleta tanason kiran sunanta amma bata iya bude bakinta sbd she's very weak. Sake yunqurawa takeyi na son dawowan jannah din amma batada karfin hakan... Ba tsammani jannah taji ankama hannunta cikin nutsuwa batareda ance komaiba. Cak ta tsaya batareda ta juyoba sbd sanin shi dinne tinda basa tareda kowa a dakin hakama girman hannun da yanayin yanda dumin tafin hannunsa ya shigeta ya tabbatar mata da ba Falaq bace. Shiru sukai dukansu kafin ta juyo ahankali tareda dagowa ta kallesa shi kuma bai juyo ya kalletaba falaq dake zubarda hawaye har lokacin yake kalla zuciyarsa na susa da kukan datake faman yi. Sake mata hannu yayi Ahankali ganin ta fahimci abinda yake nufi ta koma dayan gefen Falaq din ta zauna tana cigaba da share mata hawayenta. Zaunawa yayi Ahankali a sofa yana kallansu su duka biyun kallan nutsuwa kafin ya bude baki kai tsaye yace "Falaq meyake damunki? Meye kikewa wannan kukan? Akwai abinda yake miki ciwo ne? Girgiza kai tayi ahankali tana kallansa a marairaice. Tea da abinci tareda ruwa me dumi Fiddausi ta shigo dashi ta ajiye a table wanda jannah ta zaunar da ita ta fara bata tanasha ahankali sbd akwai yunwa sosai a tareda ita. Shiru yayi yana kallansu harta gama bata abincin tana goge mata baki kafin ta kamata suka shiga toilet shikuma ya dan fita sbd amsa waya a natse bayason hayaniya komai kankantarta a dakin falaq din sbd tattalin samun lafiyanta. Ko tsayuwa Falaq din bata iyayi sbd idan aka samu collapse irin haka a ciwonsu dukkanin karfi da kuzarinka tafiya yake gaba dayansa sai bayan dan lokaci yake dawowa. Wanka ta taimaka mata tayi wanda ya sakata jiqewa gabaki dayanta kayan jikinta suka jiqe sosai dan haka dole daga can itama rigar wankan falaq ta sako wadda tai mata kadan sosai duk da tayi mata amma tai mata guntuwa sosai dan kadan ta sauko a cinyoyinta hakama daga saman bata wani rufeta sosaiba amma bata damuba suka fito sbd ba kowa sai su kadai. Falaq ta samu dan karfin jikinta sbd wankan ya dan sake mata jikinta dan haka itama rigar bathrobe din ce a jikinta amma ita sbd tata ce daidai tai mata ta rife mata yanda ya kamata. Suna fitowa daga toilet taji sanyin Ac ya kado musu sosai har saida tsikar jikinta ta tashi ta kalli inda remote din yake tana dan sakin falaq ta nufesa dan rage sanyinsa sosai kodan falaq din da babu lafiya duk da itama bata wani son sanyin sosai. Vibrating na waya taji daga bayanta wanda ya sakata juyawa da sauri tagansa a zaune yana kallan rigar dake jikinta a natse. Kanta taji yayi mugun sarawa ta saki falaq gabaki daya tana kokarin juyawa daga ita har falaq din suka zame sbd da sakinta da yanda taja kafarta da sauri zata juya lokaci daya ta ja da kafar falaq din wadda batada karfi ko kadan dan haka baida zabin daya wuce taresu su biyun sedai ita yana tareda kofar toilet din ya koma da ita gabaki dayanta yana barin falaq wadda ya tsayar jikin bango sbd Sayd daya sako kai dakin tareda dr Sameera. Falaq dake kusa kofar toilet din ta janyo tana kallan Sayd da Dr Sameera dake kallanta. A cikin toilet din cikin zafi ya dago xai mata magana idaniwansa suka sauka akan gaban rigar data bube kadan Tabon aikinta seti da zuciyarta ya bayyana baro baro wanda ya saka zuciyarsa Skipping bugawa idanuwansa na kasa daukewa daga gurin har lokacin suna hade da junansu. Yanda zuciyarta ke bugawa kirjinta na sama yana kasa ya xubawa dinkin setin zuciyarta tasa zuciyar na bugawa idanuwansa sunyi jajir. Jin tai bugun zuciyar nata itama yana tsananta ta dago idanuwanta ahankali ta kallesa a lokacinda ba zato taji saukan tafin hannunsa akan zuciyarta wanda ya saka kirjinta bugawa da karfin gaske.. Bugun farko na zuciyar Ummitah dayaji a tafin hannunsa baisan lokacinda ya rintse idanuwansa ba yana sake matseta jikinsa hannunsa dake kan kirjinta yana wata irin rawa me sanyin data sakata kasa tsayuwa kafafunta na sanyi tana neman zubewa a gurin ya sake riqeta ajikinsa ruwan wankan jikinta na shigewa jikinsa. Qwacewa tafara kokarin yi wanda ya sakasa bude idanuwansa da sukai jajir suka sauka akan fuskanta yana mata kallo tsanarta na gauraya zuciyarsa sbd Jin bugun zuciyar 'yar uwarsa a kirjinta ya dawo masa da radadin rashinta sabo a zuciyarsa. Sakinta yayi batareda y dauke idanuwansa akantaba ta fadi qasan toilet hannunta na buguwa sosai amma bata dagoba ta kallesa duk da radadin datake ji hannun. Rigar jikinsa ya zare ya jefa mata ya juya yabar toilet. Sayd da baisan yana ciki ba yana ganinsa ko kofar toilet din bai sake kalla ba ya juya yabi bayansa batareda ya sake cewa komaiba akan maganar dayake yi da dr Sameera akan ciwon falaq dayake gabatar mata da record dinta na komai. Dr Sameera itama kasa cewa komai tayi tabi bayansa da kallo Bugun tata zuciyar itama yana qaruwa sbd ganin lafiyayyar farar fatarsa dake daukan ido da kakkarfan jikinsa daya gama budewa sbd geamin. Falaq kuwa kofar toilet ta xubawa ido tana jiran fitowan Jannah wadda hannunta ke mata tsananin azaba. Hawaye ta fara sharewa kafin ta miqe ta iya saka rigar da kyar ta fito. Juyowa dr Sameera tai tana kallanta da sauri sedai ta boye mamakinta har Jannah din taje ta dauki wani abu a cikin kayan falaq ta daura a jikinta ta fice ta nufi dakinta hannunta na mata wani irin ciwo. Tana isa dakinta kayan jikinta ta cire daqyar ta iya saka wasu kayan sai kawai ta zauna ta fasa kukan azaba da damuwan datake ranta. Sai datai sallan azahar ta fito jiki a mace taje ta sake duba falaq ta gaida mama ta koma daki. Bata fito cin abincin rana ba sedai Fiddausi takai mata daki. Bata iya cin komaiba kwance taje tana fama da wani irin azababben ciwon hannu da zazzabi. Sai yamma ta fito taje gurin falaq data warware ba laifi. A gurinta ta zauna duk da tana jin jikinta bata nuna ba ta jin dadi ba ta ringa kulawa da Falaq din har dare ta lallaba ta koma daki ta kwanta. Washe gari falaq ta tashi lafiya kalau kaman batai ciwoba sedai fushi take da daddynta tace saiya shirya da Jannah. Jannah ahankali ciwon yafara cin karfinta har lokacin ita kadaice take wahalanta a daki bata iya bacci kwana takeyi tana kukan azaba da damuwa batareda sanin kowaba. A haka su anty maryam suka taho gidan duba falaq itada babbar yarta Fadilah wadda ta gama service dinta aiki mamanta keso tayi a karkashin AZIZ wanda baa riga anfadawa ba amma dai ta saka Alh saad ya masa magana. Wuni sikai a gidan har suka tafi jannah bata fito ba bayan gaisawan da sukai kafin ta shige. Bata san anan fadilah zatai kwana biyuba saida ta fito da daddare ta ganta a dakin Falaq suna fira. Falaq na ganin jannah ta taso tana kallan cikeda kulawa tace "Jan kanki ya dena ciwon? Gyada mata kai tana zaunawa dan fitowa tai ta ragewa kanta azaba dan haka kallan Fadilah din tai tace "Ashe kina nan?? "Eh zan dan kwana biyu ne na huta kafin na fara aiki a LIMBAs" Gyada kai jannah tai kawai tana miqewa dan komawa dakinta kwata kwata ta rasa meyake mata dadi. Tana komawa daki wayarta ta dauka ta saka kiran Dad yana dauka hawayen datake riqewa suka ringa tsiyayo mata amm bata bari ya gane hakanba sukai yar fira ta aje ta kira mimi itama haka amma sam bataji sassauci abinda take jiba dan haka ta kwanta hawaye na bin gefen idanuwanta har bacci ya dauketa a hakan. Washe gari Mama ta sake tafiyar kwana biyu hakama falaq ta koma school dan haka ta koma tashin safe da wahalar aikin falaq din wadda take cewa bataso tanayi. Fadilah kuwa babu abinda take a gidan bayan zuba iko da zuba ado tana nunawa falaq kulawa da sakarwa masu aikim gidan jiki amma duk da hakan jannah ce kadai a zuciyar falaq wadda tafara shiga damuwar ganin halinda jannah take ciki na wahala da damuwa da rashin walwala, Ta bangare daya hannunta sai gaba yake sosai batareda sanin kowa ba dan harta fara kaiwa bata iya komai dashi. Wata irin rama takeyi wadda ta saka falaq shiga tsananin damuwa ta dagawa daddynta hankali ya dawo a tafiyar da yayi. A ranar daya dawo basu saniba falaq na islamiyya jannah tana daki kwance ko tashi bata iyayi da kanta saida. Fadilah ce kadai tasan dawowansa dan haka da daddare dukansu suka fito cin abinci banda jannah data dena fitowa sbd mama bata nan Fadilah itace kaman me ikon gidan yanzu tin daga lokacinda yayi mata wani irin fada da cin fuska a gaban Fadilah din da masu aiki ta dena rabar Fadilah sbd yanda take mata kallan kaman matar cushe. Falaq ce take kai mata abinci daki da kanta suna ci tare sbd yanda take cikin rashin lafiyar. Da daddaren wanka tai daqyar ta fito daga toilet ta saka rigar bacci kawai batareda ta saka komaiba ko shafawa tana kokarin kwantawa taji qarar fashewan glasses da ihun falaq me karfin gaske. Mummunan faduwa gabanta yayi ta tashi daqyar da sauri ta nufi kofa ta fito idanuwanta suka sauka aka qaton trey din abincin data dauko zata kawo mata ya subuce ya fadi gabaki daya komai ya zube glasses na cup da plate sun zube koina abincin da zafinsa ya zuba a qafar falaq din wanda ya sakata ihun daya fiddo da kowa cikin tashin hankali. Fadilah data riga kowa isowa cikin daga murya take cewa "Meyasa ita bazata fito taci abinci ba kullum kece me wahalar kai mata kaman baiwa" Jannah dataji hakan tashi hankalinta yayi sbd tasan ba qaramin baqin ciki da dacin zuciya zata kunsa ba a gurinsa dan haka jikinta ya dauki rawa ga rashin karfin jikinta zuciyarta na wani irin bugawan daya saka kirjinta mata ciwo. Basu san dashiba sai ganinsa sukai ya fito yana kallan falaq dake hawayen azaba kuma duk abinda fadilah ta fada a kunnensa.... Jannah data gansa tsananta bugu kirjinta yayi bata ko gani sosai tayi kan falaq batareda ankara da glasses din dake zubeba tayi cikinsu kai tsaye kirjinta na wani irin ciwo. Kafarta ta daga zatai ciki kirjinta ya gaza idanuwanta taji suna rufewa ta yanke jiki a gurin... Taku daya yayi ya tareta jikinsa yana hanata zubewa cikin glasses din tareda dauketa gaba daya sbd komai na jikinta ya saki alaman ta suma ko wani abin daban. Sayd ya kalla da sauri yace "Kira Doctors yanxun nan" Falaq na ganin hakan take taji ta dena jin zafin nata ciwon tafara kiran sunan jannah cikin tashin hankali tana bin bayan Daddynta daya nufi bangarensa da Jannah din wadda yake tsananin fatan babu abinda zai sameta sbd zuciyarta datake kirjinta. #MAMUH ZAFAFA BIYAR KALBIM 500 mamuhgee A DUNIYATA 500 Huguma AJIYA A DUHU 500 Billyn Abdul KIRJIN ME HANKALI 500 Miss xoxo Pay at 0022419171 AccessBank Maryam sani gummi Shedan biya 09033181070 Or mtn vtu at 09032345899*_KALBIM_* _Mamuhgee_ 71 *UMMU_MAHNOOR LUXURIES* (Best luxuries shop) 08034469681 08135142610 Aslm Alaikm ina kuke masu neman luxuries na kayan alfarmar kece raini? Ina masu son su saka sitirar alfarma ta zamani ta manyan mata masu aji da zaa kalleki kallo daya asan sitirar alfarma e kika saka? Shin kunsan me ake nufi sa kayan asalin yan gayu da nuna gayu? Sitirar Alfarma kikeson sakawa? Sitirar da kike ganin manyan mata da ita? Sitirarda zakiyi gayun sallah dake da yaranki a dauka waje kikaje da kanki kika siyota? To kizo ga damarki ta sameki sbd UMMU_MAHNOOR LUXURIES ta kawo miki sauki har gida, Karkice se masu kudi ke iya siya har kema me yar dama zaki samu naki da saukin kudi kuma best quality da kalar zamani data yan gayu, Nidai Mamuh nace duk wadda ke son a buga gayun sallan bana da ita da 'yayanta to tazo gurin UMMU_MAHNOOR LUXURIES tai siyayyar sallanta harma zuwa gaba dan nasan zakuji dadi da fahimtar abinda nake fada akan kayanta💯💯 Abubuwan da zaki samu a gurinta with the best quality na wayayyun mata masu aji yan gayu sune; Atampopi Laces Shadda Materials Shoes Bags Veils Trolleys Jewellerys Oil perfumes Numbers 08034469681 08135142610 Handles Instagram @ummu_mahnoor_luxuries TikTok username @ummu_mahnoor_luxuries Facebook ummu_mahnoor_luxuries *********** Sakin baki fadilah tayi tana bin bayansu da kallo zuciyarta na nauyi, Fiddausi kuwa da daman take cikin damuwa da tsananin tausayin halinda jannah take ciki duk tsawon lokacin jin tai jikinta yayi sanyi. Falaq dai tini tabi bayansu kusan a tare suka isa tana jin nata ciwon ma kaman ta dena jinsa. A palonsa ya kwantar da ita kan kujera kafin ya dago kanta falaq tai saurin saka mata pillow tana kallan fuskanta datai fayau. Shi kansa fuskan tata ya zubawa idanuwansa yana kalla a natse, Duk da baya mata kallan tsaf sosai bai wani riqe yaya komai nata yake ba yasan tana cikin wani hali sbd yanda tai wani irin pale da rama sosai tareda sauyawa sosai. Dauke idanuwansa yayi Ahankali daga kanta yana maidawa kan falaq datake kallanta cikeda damuwa da tsoron kada komai ya samu jannah din. Hannu ya miqawa Falaq din yana hana yanayinsa bayyana ta gurinsa tana fasa kuka ahankali tana cewa "Daddy Jannah batada lafiya sosai,.ta dade batada lafiya, Ko abinci bata iya fitowa taci, Hannunta ya karye sosai take fama dashi nayita cewa muje asibiti or a kira dr sai tana cewa aa kaman tana gudun abinda zakace ne, Tana cikin damuwa sosai kwata kwata bata cikin farin ciki, Daddy pls ka kula da ita ka bata farin ciki, I really love as my mum,bazan iya rabuwa ita ba dan haka daddy dan Allah ka sota sosai ko dan sbd yanda nake kaunarta itama take kaunata pls Daddy na rokeka" Qarasa zancen tayi hawaye masu tsananin zafi na gangaro mata wanda ya sakasa maida idanuwansa ahankali akan jannah din wadda bata motsi har lokacin. Kallon tsafta yayiwa fuskanta tsawon mintina kafin ahankali ya gangaro da idanuwansa akan kirjinta setin zuciyarta ya tsayar dasu agurin yana radadin a zuciyarsa dayake tattare da yanayi biyu, Jin yake kaman ya kasa, Jin yayi yana neman tsanar kansa sbd zuciyarsa na kokarin failing Ummitansa. Hannunsa ba zato a natse falaq ta dora akan hannun Jannah din ta dora nata akan nasa tana cewa "Daddy pls for my sake ka karbeta a matsayin matarka,wlh tana tsananin sonka Daddy, Tana enduring da hadiye komai ne sbd son datake mana ni da kai, Daddy zakaso wasu familyn suyi treating dina kaman yanda mukaiwa Jannah wadda tanada gata da power ta family irin wadda nake dashi?????? Dago idanuwansa da sukai ja yayi ya kalli falaq din yana shigar da ita jikinsa ya rungume yana kokarin dedeta bugun da zuciyarsa takeyi akan zancen da falaq din ta fada kawai akan ayi masa treating dinta kaman hakan zai iya aikata abinda hankali bazai daukaba. Hawayene suka sake zubowa falaq tana jin kwata kwata basuwa tsananin so da kaunar da jannah take musu ba bayan ta zabi juyawa wanda ya taso da kaunarta shekaru masu yawa baya akan tsananin son datake musu itada Daddynta, Su kansu iyayenta sun zabi juyawa nasu baya suka zabi basu ita sbd farin cikinta amma gata ta qare a hannunsu masu aikinsu ma sunfita jin dadi. Dr Sameera ce ta iso gidan cikin gaggawa sbd yanda sayd ya daga mata hankali da kira da buqatanta a cikin tsananin gaggawa. Knocking kofar palon yayi wanda ya saka Falaq miqewa da sauri ta nufi kofar da fatan Dr ne ya iso. Ahankali ya dawo da idanuwansa akan Jannah din ya zare tsadaddiyar D&G jacket dinsa ya rufe cinyoyinta farare tas dasuke bayyane sbd rigar jikinta batada tsayi sosai. Dr Sameera ce ta shigo palon Sayd kuwa baima shigoba ya koma yana tinanin Allah yasa ha matsalar zuciyarta bane sbd irin silent pain din dayake hangowa a idanuwan AZIZ ya tabbatarda jin yake kaman kaman Ummitah ce a gabansa wani abu zai sake samunta sbd dena bugawan zuciyarta kaman sauran abinda ya rage musu na Ummitah ne yabarsu dan haka zuciyoyinsu sukai nauyi da wata damuwar da basusan ta ina take cikesuba. Dr Sameera kuwa duk taimakon da zata bawa Jannah din ta bata babu alaman suma ne kawai dan haka dole ta buqaci suyi asibiti da ita cikin gaggawa sbd bugun zuciyarta gaba daya ba daidai yake ba. Hakan da dr Sameera ta fada ya saka AZIZ din zubawa Jannah din idanuwansa yana jin kaman ya hana a kaita asibitin a hakan sedai kuma bazai bari zuciyarta ta dena bugawaba. Falaq da jikinta har rawa yake sbd tsoron rasa Jannah da sauri ta kallesa zata kira sunansa bai tsaya jiran komaiba ya shiga bedroom dinsa ya dauko daguwar rigarsa jallabiya me shegiyar kyau da qamshi ya zirawa Jannah din ya dauketa gaba dayanta ya nufi kofa suka biyo bayansa. Sayd na hangosa ya nufi waje da sauri kafin su iso ya tada mota tareda zuwa daf da kofar fitowa main palo ya tsaya Latif ne ya bude motar da sauri shima jikinsa na rawa. Da mugun speed Sayd yabar harabar gidan da mota bayan securities sun bude musu gate tini. Dr Sameera falaq tabi sbd yanda ta daga hankalinta ko anbarta kuka zataita yi. Suna barin gidan Mama na isowa da sabon driver dinta yaje ya daukota Airport. Cikin mamaki take tambayar Su jannah din da falaq Fiddausi ce ta sanar mata komai cikin mutuwar jiki. Itama maman damuwa ta shiga tana fidda waya kiran AZIZ sedai harta yanke bai daga ba. A asibiti suna isa da gaggawa akai emergency da jannah din wadda aka fara kokarin dawo da numfashinta da baya fita sukeyi. Zaune yake a gurinda aka tanadar masa na jira Sayd na tsaye a bayansa yana kokarin neman hanyar da zasu samu history record na ciwonta sbd dole sai dashi zaa samu damar sanin yanda zaa bi da yanayinta. Falaq na gefen Daddyn nata idanuwanta sunyi zuru na jiran tsammani. Zaman awa kusan biyu zuwa uku sukai kowa da abinda yake zuciyarsa kafin Dr Sameera ta fito tareda wani dr Ashir Ya kallesu yana jiran abinda zasu fada. Numfashi sauke suna kallansa kafin cikin girmamawa da bayyanarda yanayin da ake ciki Dr Ashir dinne yace "Numfashinta ya dawo hakama bugun zuciyar ya dan samu sedai ga dukkanin alamun da muka gani shine bugun zuciyarta is very weak wanda hakan na nuna Alamar heart patient ce so for now saita farfado munsan komai akan yanayinta zamu iya dubata dakyau, Sai kuma hannunta da shima anriga an dubasa anji dashi insha Allah dan haka yanzu muyi fatan farfadowanta a lokaci" Numfashi mara sauti sosai Sayd da Falaq suka sauke a lokaci daya yana kasa cewa komai. Shi kuwa dago idanuwansa kadai yayi ya kalli Dr Ashir din a tsanake ya furta "Thanks Doc" Shiru sukai dukkaninsu kowannensu da tinanin dayake zuciyarsa sedai babu wanda yace komai sai falaq data lafe gefen jikinsa idanuwanta da jikinta sunyi sanyi. Har dare bata farka ba dan haka ya buqaci su koma da ita gida a hakan aci gaba da bata kulawan a gida sbd babu yanda zaayi abarta asibiti ita kadai gashi har lokacin Zaadens basu saniba. Ambulance ce ta dawo da ita gida a daren. A dakinta aka kwatar da ita ya dauki nurses kwararri guda biyu dan kulawa da ita duk da ga mama ga Fiddausi amma dai nurses din sune zasufi sanin abinda ya kamata. Saida aka gama mata komai aka falaq ce ta rufeta ta abin rufa me taushi ta zagaya ta kwanta gefenta sbd bazata taba iya kwana daban tabar Jannah a wannan halinba. Shi kansa saida Falaq din tai bacci a gefen Jannah din kafin ya same sauke numfashi me dumi da gaba daya ayau din sai yanxu ya samu daman sauke numfashi. Jannah ya saukarwa idanuwansa ya xubawa idanuwanta dake rufe ido yana kallan yanda sukai zurfi.... A bakinta daya bushe ya gangaro da idanuwansa ya zuba musu suma kafin ya dauke su ya maidasu akan hoton dayake bedside dinta a qaramin flame guda uku ajiye. Hoton Daddynta ne na farkon shi kadai cikin Kamala da cika ido kaman asalin mutumin kirji.. Dauke idanuwansa yayi yana saukarwa akan dayan frame din hoton Mimi da Maheer da saleem ne da Ammar Dukansu da fararen shirts da blue jeans sai Ammar daya saka fcap. Zubawa hoton karshe ido yayi wanda shine hoton Ammar Zad shi kadai sanye da Black Armanis..... Tsayar da idanuwansa yayi akansa yana masa kallo biyu masu qarfin gaske na farkon shine kallansa a matsayin wanda ya kashe masa tasa yar uwar da hannuwansa ya zare zuciyarta daga kirjinta ya sakawa tasa macen wadda take matsayin Matarsa a yanzu amma hotonsa ne a gefen gadonta tana kwana dashi tana tashi dashi. Miqewa yayi tareda ficewa a dakin yana bawa nurses daman su shiga su sake dubata kafin su wuce dakin da aka saukesu. Kai tsaye hanyar palonsa y nufa yana sako kai ciki Fiddausi na ajiye tray din tea da zuman data kawo masa ta juyo ta fice cikeda girmamawa. Kai tsaye Bedroom dinsa ya shige yana zare rigar jikinsa ya nufi hanyar toilet yana zare wandon yaja towel ya qarasa cikin toilet ya sakarwa kansa ruwan dumi yana rufe idanuwansa hannuwansa na dan yin rawa alaman yanayinsa zai motsa amma yana kokarin hana hakan. Ya dade sosai a ciki yana fama kafin ya fito ya shirya cikin kayan bacci masu santsi da tsada ya haye gadonsa ya kwanta batareda yasha tea din da aka kawo masa ba sbd kansa dayayi nauyi. Washe gari har 10 bai fito ba sbd ciwon kan daya tashi dashi dan haka sai guraren 11 ya fito kuma kai tsaye dining ya nufa. Mama dake palo tareda fadilah kallo daya tai masa ta fahimci yanayinsa dan haka cikin kulawa ta amsa gaisuwansa batareda wani dogon zancen ba da zai iya kara masa ciwon kai. Fadilah kuwa itace ta miqe tabisa har Dining tayi serving dinsa abinci cikin kulawa sosai da kokarin nuna kamun kanta. Bai cika kallo ba dan haka bai wani yi mata kallan Arzikiba yafara breakfast dinsa a natse. Falaq na dakin Jannah data farfado sedai kwata kwata ba karfi ko kadan a tareda ita hakama ga hannunta daya a daure bata iya komai dashi sedai da dayan. A karo na kusan biyar falaq ta fito tana kokarin nufar palonsa sake dubosa Mama tace mata "Ya fito yana dining room,yaya jikin jannah din?? Juyawa zuwa dining tayi cikin farin cikin son sanar dashi jan din ta farka tacewa mama "Taji sauki wanka ma zatayi" Hamdala mama ta sake yi sbd tin safe itama take yawon dakin har bayan farfadowan jannah din, Dining room din take kokarin nufa sai gashi ya fito a natse kwarjinsa na sake cike idanuwan Fadilah da Fiddausi harma sa maman. Kama hannunsa tayi cikeda murna tace "Goodmorning Besty, Albishirinka,My Jan ta farka tin dazu fa" Kallanta yayi a natse batareda nuna mahimmancin zancen garesaba ya bude baki yace "Hakanne ya sakaki farin ciki sosai haka??? Gyada kai tai da sauri tana sake riqesa tace "Wanka ma takeson yi tin dazu sbd ta samu karfi kadan amma ta kasa cire kayanta sbd hannunta daya nima nayi na kasa tin dazu banason taci gaba da wahala so Muje ka tayata Daddy banason ta fama hannunta" Tsit palon sukaj hadda Sayd dayake zaune gefen mama bai dagoba yaci gaba da duba abinda yake dubawa cikin ipad din hannunsa. #MAMUH ZAFAFA BIYAR KALBIM 500 mamuhgee A DUNIYATA 500 Huguma AJIYA A DUHU 500 Billyn Abdul KIRJIN ME HANKALI 500 Miss xoxo Pay at 0022419171 AccessBank Maryam sani gummi Shedan biya 09033181070 Or mtn vtu at 09032345899*_KALBIM_* _Mamuhgee_ 72 *UMMU_MAHNOOR LUXURIES* (Best luxuries shop) 08034469681 08135142610 Aslm Alaikm ina kuke masu neman luxuries na kayan alfarmar kece raini? Ina masu son su saka sitirar alfarma ta zamani ta manyan mata masu aji da zaa kalleki kallo daya asan sitirar alfarma e kika saka? Shin kunsan me ake nufi sa kayan asalin yan gayu da nuna gayu? Sitirar Alfarma kikeson sakawa? Sitirar da kike ganin manyan mata da ita? Sitirarda zakiyi gayun sallah dake da yaranki a dauka waje kikaje da kanki kika siyota? To kizo ga damarki ta sameki sbd UMMU_MAHNOOR LUXURIES ta kawo miki sauki har gida, Karkice se masu kudi ke iya siya har kema me yar dama zaki samu naki da saukin kudi kuma best quality da kalar zamani data yan gayu, Nidai Mamuh nace duk wadda ke son a buga gayun sallan bana da ita da 'yayanta to tazo gurin UMMU_MAHNOOR LUXURIES tai siyayyar sallanta harma zuwa gaba dan nasan zakuji dadi da fahimtar abinda nake fada akan kayanta💯💯 Abubuwan da zaki samu a gurinta with the best quality na wayayyun mata masu aji yan gayu sune; Atampopi Laces Shadda Materials Shoes Bags Veils Trolleys Jewellerys Oil perfumes Numbers 08034469681 08135142610 Handles Instagram @ummu_mahnoor_luxuries TikTok username @ummu_mahnoor_luxuries Facebook ummu_mahnoor_luxuries *********** Mama dagowa tayi ta kalli falaq din kaman ta janyota ta bude kanta ta saka mata sanin ya kamata sbd kai tsaye take maganar komai bata tsayawa sanin me take fada ba ruwanta. Fiddausi silalewa tayi ya koma kitchen, Fadilah kuwa AZIZ din ta sata kallansa zuciyarta na harbawa sbd bata fatan ya ya tafi taimakawa jannah din sbd a sani da fahimtar dataiwa auren nasu da kyau da kyau bai taba kallan Jannah din a matsayin matarsa ba dan haka ba lallai sun taba samun intimacy ba. Muskutawa ta dan yi kadan tareda kallan Falaq tana dan sake fuska tace "Ayya ai duk bamu saniba da duka gami xamu taimaka mata, Bara naje na taimaka mata din" Miqewa take kokarin yi Falaq tai saurin cewa "No,Daddy ne zai tafi ni banason kowa ya taimakawa Jannah daga ni sai Daddy se Fiddausi" Da sauri fadilah tace "To bari na kira Fiddausin taje ta taimaka matan" "I said no banason kowa a yanzu, Daddy ne zaije ai daman bai dubata ba yau da safen" Mama da zancen yake neman sakata kunya kallan AZIZ din dayake barin palon xuwa hanyar nasa palon tace "Kaje ka dubata mana AZIZ taji jiki fa yarinyar kuma ya kamata a sanar da iyayenta duk da zanji kunyar su ganta a yanda take yanzu" Falaq da tini tai raurau zata fara masa kuka ya kalla yana juyawa zuwa hanyar dakin Jannah din da baida niyar sake shigansa. Yana shiga dakin ta bude idanuwanta dake rufe ahankali ta kallo kofa tana motsawa kadan. Ganinsa ya sanyata fara kokarin tashi zaune daga jinginen datake a tsakiyar gadon tanajin gabanta na dan faduwa da fargaba. Kallo daya yayi mata ya dauke idanuwansa akanta yana Nufota. Ganin ya nufota ya sakaya yaye rufanta tana ziro kafafunta kasa ta miqe hannuwanta na dan rawa sbd fargaba da shakkarsa data riga ta shigeta. Yanda kafafunta ke rawa yasaka tsayuwar ta gagara tana neman zubewa ya sake riqota a karo na biyu yana kallan idanuwanta da itama shi ta dago tana kallo cikeda fargaban ko fada zaiyi mata. Yanda take kallansa tsoronta na bayyana hakama yanajin yanda zuciyarta ke bugawa a kirjinsa ya sakasa dauke bude baki har saida iskan cikin bakinsa ta bugi fiskanta ahankali da wani sanyayyan qamshi mouth wash dinsa da sauti me nutsuwa ba hayaniya yace "Kina koyawa yarinyana sakani yi miki abinda kikeso a tilas ne??? Kina amfani da ita ne?? Girgiza kai tai a hankali tana sake kallansa idanuwanta na kokarin cikowa da hawaye. Cikin tsakiyar idanuwanta ya kalla har lokacin tana jikinsa yana karban bugun zuciyarta a nasa kirjin. Bai sake cewa komaiba ya saketa ahankali tareda kama rigarsa datake jikinta har lokacin tai mata yawa sosai yafara dagowa ahankali yana kallan cikin idanuwanta. Jin rigarsa datake jikinta zai cire ya sakata saurin sauke idanuwanta ahankali daga kallansa tana jin bugun zuciyarta na qaruwa. Rigarta qarama ce ta ciki taji tabi rigar dayake kokarin cire mata da sauri ta dora tafin hannunta akan hannunsa tana rufe idanuwanta ahankali kanta a qasa. Dumin dayake cikin tafin hannunta ya sakasa dagowa ya kalli hannun nata dayake kan nasa ta dafe kafin ya zuba mata mayun idanuwansa akan fuskanta data kasa bude ido ta kallesa. Sake damke hannunsa tai zuciyarta na bugawa da karfi sbd jin idanuwansa akanta suna azabtar da ita. Sake jan rigar tayi zuwa sama har lokacin hannunta yana kan nasa ta kasa daukewa sbd tana jin cinyoyinta na bayyana. Yana dago rugar tana zuwa daidai gurin da cinyoyinta suka qare ta bude idanuwanta ahankali ta kallesa cikin tsananin sanyi da wata lallausan muryanta datai laushi can qasa ta bude baki tace "Please" Dakatawa yayi yana kallan bakinta da yayi maganar kaman ba ita taiba. Ahankali yakai idanuwanta ya kalli abinda take nufi, Kallo daya yayiwa cinyoyinta dake wani daukan idon haske da lafiyarsu ya dauke idanuwansa yana sakin rigar gaba daya tareda sakinta tai saurin zaunawa vakin gado itama tana kasa sake kallansa zuciyarta na narkew da qamshinsa daya gama shigarta tako ina. Juyaw yayi zai fice daga dakin daidai falaq na knocking tareda budewa ta shigo tana kallansa tace "Daddy baka taimaka mata ba? Kama hannunsa tai suka dawo dashi da ita suka zarewa jannah din rigar batareda jannah din ta bari an zare data cikinba dan haka suna zarewa ya juya yabar dakin sbd rigar jikinta ta cikin ko bra barada ita ta lafe jikinta sosai tana bayyanarda abinda idanuwansa basu taba gane masa. Su kuwa toilet Jannah ta tashi ta shige tana jin kaman ta samu dan karfin jikinta sbd ba qaramin so zuciyarta kewa AZIZ LIMBA ba wanda ko tsayuwa yayi a gabanta jin take kaman zuciyarta ta gama samun abinda takeso. Shi kuwa yana fitowa palonsa ya nufa ya kira Sayd. Tsayuwa Sayd yayi gabansa yana jera masa bayanin Dr Abraham yana inda suke jiran ya baro su kamasa haryanzu bai baroba dan haka suna buqatan qarin lokaci. Shiru AZIZ din yayi yana sauraron bayanin Sayd wanda bayajin zai iya jiran lokacin da ake magana sbd komai zai iya lalace masa, Zai tsani kansa tsana mafi muni idan yabari wani lamarin ya shigo ya lalata masa aikin daya kawosu, Bazai taba yafewa kansa ba idan har ya sassautawa duk wanda yakeda hannu a kisan Ummitah dan haka bazai jira bata lokaci ba zaiyi abinda ya kawosu su tattara su koma sbd zuciyarsa bazata taba karban wani baqon yanayiba kowane irine. Dago idanuwansa da sauka dan sauya yayi fuskansa ba sakewa kai tsaye cikin kamewa yace "Zaadens zasusan batada lafiya sosai dan haka da kansu zasu nema zuwan likitocinta duka a cikin gaggawa wanda basu kowa bane face su ABRAHAM da 'dansa sai dayan da muke nema wato KEN, Dukkaninsu zasu bayyane idan Zaadens hankalinsu ya tashi akan ciwon zuciyar da aka dade rufe maganar ciwonta" Sayd ne ya dago ya kallesa cikin girmmawa yace "Amma a yanayinta yanxu ta samu dan saukin da zai hanasu shiga tashin hankalin da ake buqata" Batareda ya kalli Sayd dinba cikin nutsuwa yace "Zan bata wani heart Attack din dazai kawo hakan" Gyada kai Sayd yayi yana cewa "Komai zai zama ready akan hakan insha Allah" Gyada kai kawai yayi yana dan dafe goshinsa da yayi nauyi kadan. A can dakin jannah din tai wanka ta dan samu kwari ta fito da taimakon falaq ta dan shirya cikin doguwar riga mara nauyi ko wahalan sakawa ta ranka sallolin dake kanta Fiddausi da falaq ne suka bata abincin cikeda kauna da kulawa ta koshi tasha magani bacci me dadi ya dauketa tana dan samun nutsuwar zuciya. Har dare su Fiddausi da falaq ne ke bata kulawa sosai harma da mama da itama take nuna kaunar datake mata sosai wanda ya sakata sake samun karfi sosai tana sake warwarewa. Dr Sameera da dr Ashir sunzo sun dubata dan haka ta sake samun saukin sosai, Da daddare bayan ya dawo gidan babu wanda ya sani saida ya fito dinner a lokacin ne sukasan da yana gidan gashi kusan 9 tayi. Falaq ce ta rakasa dining yanacin abinci tana masa labarin yanda jannah take samun sauki yana sauraronta batareca yace komaiba sbd duka zancen Falaq din yanxu na Jannah ne. Yana gamawa ta jasa suka nufi dakin Jannah din wadda take zaune sanyeda riga da wandon bacci masu santsi batar qarasa rufe botiran gaban rigarta ba tana ta kasa sbd hannunta daya da baya aiki. Qamshinsa daya shiga hancinta ya sakata qin juyowa sbd ta kalli wanda ya shigo sbd tasan shi dinne. Ahankali ta saka hannunta daya ta dafe gaban rigarta daya bude sbd bata saka botiran ba gashi babu bra a jikinta. Falaq kallan Daddyn nata tayi zatai magana Fiddausi tai knocking kofar a dan kiyaye cikin nutsuwa da gudun masa hayaniya tace "Mama na kiran falaq" Juyawa falaq tai ta nufi kofa ta fice tana cewa "To ni me zan mata" Tana rufe kofar numfashin jannah yayi sama tanajin bazata iya tsayawa ba a dakin itama ta miqe ahankali tareda juyowa tana jin son barin dakin itama wayarta tayi haske tana vibrating akan table din dayake gabansu. A tare suka saukan da idanuwansu ahankali kan wayar video call ne daga Ammar Zad. Kasa motsawa tai tana kallan wayar gabanta na dan faduwa. A natse ya dauke idanuwansa daga kan wayar yana takowa zuwa gareta. Tsananta shiga faduwan gaba tayi dan haka ta cire hannunta daga gaban rigarta data dafe ta miqa kan wayar da sauri ta dauka sbd tasan daukan wayar kawai zai saka AZIZ barin dakin shikuwa ba tsammani ya dora hannunsa yana hade kirjinta da nasa yana dafe rigar data sake tana mantawa sbd rikicewan datai. Hakan ya sakata sakin wayar yannunta kan sofa data bawa Ammar daman ganinta Manne a jikin AZIZ LIMBA yana mata wani irin kallo fuskansa ba sakewa ko kadan. Kirjinta ta kalla a hankali taga rigar ma kaman ta bude gaba daya amma komai baa gani nata sbd yanda kirjinsa ya rufeta gabaki dayanta hannunsa daya yana zagaye da ita. Dagowa tai ta kallesa tanason janyewa yayi mata wata irin riqon daya sakata rintse idanuwanta cikin zafi. Ahankali yakai bakinsa a kunnenta zaiyi magana dumin numfashinsa daya fara sauka a cikin kunnen ya sakata qanqamesa batareda tasan tayi hakan da wata irin murya me tafe da zafi a natse yace "Kinada hankali kuwa? Are really ok a cikin kanki kuwa? Kin saba hakanne kokuwa? Ashe rashin tarbiyan naku ya wuce hankali har haka? A tsakanin ni dashi waye kike kokarin nunawa jikinki da zaki dauki wayarsa a wannan yanayin??? Kokuwa ke dashi din k...... Bai qarasaba zuciyarta ta kasa daukan maganganunsa sbd yanda jikinta ke rawa sosai cikin mummunan yanayin yanda kalamansa ke dukanta. Wani mummunan bugu zuciyarta keyi hannuwan ya tsananta rawa ta zube a jikinsa hawaye na gangarowa gefen idanuwanta. Ammar da shedan ya hanasa kashe wayar yana ganin yanda AZIZ yake fada mata magana a kunnenta har jikinta ya sake batareda yasan meya fada mataba. Kashe wayar AZIZ ya miqa hannu yayi yana dawo da kallansa kan fuskanta kalaman daya furta mata suna tafasa cikin kwakwalwansa ya dauketa cak ya dora a gado ya ciro wayarsa ya kira Sayd yace ya kira doctors ta samu collapse. Yana kashe wayarsa wayar Dzad ya saka kira take ya sanar masa Jan din tayi collapsing a karo na biyu tsakanin shekaran jiya zuwa yau. Zaune Dad din yake ya miqe tsaye a hankali yana cewa "Wat? A cikin kwana biyu tai collapsing so biyu baa sanar mana ba? Heart patient ce ita fa, Innalillahi wainnna ilayhi rajiun" Maheer da Daddy mahmoud dasuke tareda Dzad din kallansa sukai kowannesu na jiye wayar hannunsa gefe. Ammar kuwa Daqyar zuciyarta tabar idanuwansa gani sbd tafasa da radadin da zuciyarsa ke yi ya iso palon ya tadda abinda ake fada. Wani yawun tsananin tashin hankali da baqin ciki ya hadiye Dad ya kallesa yana cewa "A kira su Dr Abraham sbd kasan babu wanda zaa bari ya dubata dole zaa buqaci record na ciwonta wanda babu saka hannun familyn donor dinta a ciki so kota halin yaya bazaa bari wasu likitas din ba su dubata sai nata, Amma kafin nan muje ka fara dubata kai kanka" AZIZ Yana gama waya da zaadens Sayd ya kira yace "Ka shirya komai Ken na sauka Nigeria nake buqatansa kafin ma Abraham din" Kashe wayarsa yayi yana zaunawa bakin gadonta ya zubawa fuskanta ido yana jin zuciyarsa na nauyi. #MAMUH ZAFAFA BIYAR KALBIM 500 mamuhgee A DUNIYATA 500 Huguma AJIYA A DUHU 500 Billyn Abdul KIRJIN ME HANKALI 500 Miss xoxo Pay at 0022419171 AccessBank Maryam sani gummi Shedan biya 09033181070 Or mtn vtu at 09032345899*_KALBIM_* _Mamuhgee_ 73 *UMMU_MAHNOOR LUXURIES* (Best luxuries shop) 08034469681 08135142610 Aslm Alaikm ina kuke masu neman luxuries na kayan alfarmar kece raini? Ina masu son su saka sitirar alfarma ta zamani ta manyan mata masu aji da zaa kalleki kallo daya asan sitirar alfarma e kika saka? Shin kunsan me ake nufi sa kayan asalin yan gayu da nuna gayu? Sitirar Alfarma kikeson sakawa? Sitirar da kike ganin manyan mata da ita? Sitirarda zakiyi gayun sallah dake da yaranki a dauka waje kikaje da kanki kika siyota? To kizo ga damarki ta sameki sbd UMMU_MAHNOOR LUXURIES ta kawo miki sauki har gida, Karkice se masu kudi ke iya siya har kema me yar dama zaki samu naki da saukin kudi kuma best quality da kalar zamani data yan gayu, Nidai Mamuh nace duk wadda ke son a buga gayun sallan bana da ita da 'yayanta to tazo gurin UMMU_MAHNOOR LUXURIES tai siyayyar sallanta harma zuwa gaba dan nasan zakuji dadi da fahimtar abinda nake fada akan kayanta💯💯 Abubuwan da zaki samu a gurinta with the best quality na wayayyun mata masu aji yan gayu sune; Atampopi Laces Shadda Materials Shoes Bags Veils Trolleys Jewellerys Oil perfumes Numbers 08034469681 08135142610 Handles Instagram @ummu_mahnoor_luxuries TikTok username @ummu_mahnoor_luxuries Facebook ummu_mahnoor_luxuries ************** Maheer ne da kansa ya nutsu a cikin daren ya kira Abraham ya sanar dashi abinda yake faruwa sbd suna buqatansa duk da Ammar yana nan amma sunsan damuwa da tashin hankali zai iya hanasa nutsuwar dubata yanda yakamata. Basu sanar da Mimi ba a cikin daren Motar Dad tareda Saleem daya jasa tabar Zaadens zuwa limbas, Motarsa na ficewa ta Maheer tabi bayansa tareda Daddy mahmoud Sai ta Ammar a bayan tasu suka nufi Zaadens din gabaki dayansu damuwa a cikeda kirjinsu da fargaban idan ba ciwon dasuke fatan sun rabu dashi bane kwata kwata yake kokarin dawowa ace itama wannan zuciyar datake kirjinta tanada matsala ko me?? Koda suka iso limbas Securities sun san da zuwansu wanda Sayd ya sanar masu tareda umarnin daya san ko LIMBA bai fadaba shine abinda yake daidai a mansion din nasu., Dan haka motar Dzad na isowa da sauri Securities suka bude masa gate ya saleem ya sako kan motar ciki, Motar Maheer ma sako kai tayi a ciki shima da gudu yana parking gefen motarsu Dzad. Motar Ammar na sako kai chief Security na Securities din gidan ya taso yana bada umarnin a rufe gate din yana kallan Motar ya qaraso fuskansa ba rahama ko kadan Kaman zai dauki rai a gurin yake jinsa da hannu yayiwa Ammar din alaman ya sauke glass. Wani kallan qyama da Mamaki Ammar din ke masa tareda tsanar duk wani abin dayake cikin limbas din da dukma wanda yake gidan tin daga kan Securities har asalin masu gidan tsana me girma yake jin yana musu sbd shi kadai yasan yanda yake jin zuciyarsa daya taho sbd Jannah amma badan hakan ba zai iya zabar zuwa ga azaba akan zuwa limbas dayake jin tsananin tsanarsa da zafinsa. Aron da bai damu da komaiba sai umarnin da aka basa dan kuwa sedai ayi ruwan albarushi a guri idan har umarni suka sauko daga LIMBA to haka zaayi kuwa koda ana mutuwa a shirye suke da mutuwa da kashewa akansa dan haka ganin Ammar din yaqi sauke glass yana jiran su bude masa gate ya saka Aron din komawa gurin zamansa yana cewa Securities din "Mamas boy da alama bai san yana bakin limbas bane, Idan bai sauke glass nasa ba daga nan har saiya gaji ya koma inda ya fito kada matansa ta qara ko inci daya zuwa gaba, Idan ya qaro gaba zuwa ciki just Shoot" Ammar dayaji abinda daya fada Dago idanuwansa da sukai jajir yayi yana kallan gate din Limbas din zuciyarsa na tafasa da narkewa ahankali sbd tinda aka haifesa ya taso cikin gata da buga lokaci tareda juya abinda yakeson ya juya yanda ransa yakeso batareda shakka ko umarnin kowaba sbd suna juya duniyarsu ne da hannunsu yanda suke sonta sbd sune ZAADENS, ZAADENS da kowa yake shakka da tsoro, Ayau shine a gaban gidan wani ana rufe masa gate tareda bada umarnin a harbesa idan ya qara gaba, Duk gwagwarmayar da yayi akan jannah da ciwonta yana tashi a banza ne ko me? Ya sadaukar da lokacinsa da kuruciyansa gurin komawa baya a karatu, Ya sadaukar da imaninsa ya koma makashin gaske, Ya sadaukar da rayuwarsa ya ture lokacin komai na rayuwarsa ya bayar duka akan macen da zai iya bata rayuwarsa amma a lokaci daya wani yana tsayar masa da dukkanin iyakansa akanta ta hanya mafi ciwo. Jajir idanuwansa sukai wani irin radadi me sanyi da ciwo na cike kirjinsa ya rintse idanuwansa hannuwansa dake riqe da steering suna dan rawa cikeda radadin dayake gauraye koina a jikinsa. Securities kuwa gabaki dayansu tsaye suke da bindigoginsu sunfi su goma babu wanda baa shirye yake da harbi ba sbd yana motsawa ruwan bullet zasuyi masa su kuma ce Shine yayi intruding dan haka sun harbesa a matsayin suspect dayayo cikinsu da mota da niyar barazana ga rayuwarsu so a taiqace sun harbesa as self defence. Su Dad kuwa Sayd ne dayake harabar gidan ya tarbesu a natse suka isa ciki. Dayake dare ya danyi su mama gaba daya sun shige dan haka kai tsaye dakin Jannah din suka nufa tana sanye da kayan sanyin da AZIZ din ya dora mata akan kayan dayake jikinta tana kwance babu abinda yake motsawa ajikinta hatta bugu da fitar numfashinta kaman babu ko daya. Dukkaninsu kallo daya sukai mata suka dago cikeda matsanancin tashin hankali da mummunan yanayi suka kalli AZIZ daya kallesu hankalinsa ba alaman ya damu da yanayinsu. Dad ne ya tsaya akanta yana kallan yanda idanuwanta sukai zurfi hancinta ya qara tsayi dosai sbd muguwat ramar datai tayi pale sosai gabaki daya kammanninta sun sauya sbd ya dade bai gantaba.... Nauyi me tsanani ne ya danne zuciyarsa ya rintse idanuwansa yana sake budesu akanta cikin tsananin sanyi ya ce "Meya sameta ta koma haka? Ta dade ne batada lafiya? Jannah ce ta koma hakan? Meyake faruwa? Maheer dauke idanuwansa daga kanta yana jin zuciyarsa na karyewa da tsananin tausayinta da jin ciwonta a cikin ransa.. Daddy mahmoud kuwa wayarsa ya fidda yana saka kiran Ammar daya kasa isowa haryanzu yazo ya duba musu ita kokuma su tafi da ita gida ayi mata komai acan sbd normally irin haka idan tai collapsing takan dauki kwanaki kafin ta farfado. Ringing wayar Ammar keyi a gefensa yana kallo da jajayen idanuwansa dake cikeda radadi ya kasa dauka sbd zuciyarsa fashewa zatai idan ya bude baki yayi magana, Barin gurin yakeson yi amma ya kasa koda motsa hannuwansa ne baya gani sosai sbd baqin ciki da ciwon daya danne masa kirji da zuciya. Cigaba da sake kiransa Daddy mahmoud keyi amma wayar baa dagawa dan haka Maheer ya fidda tasa wayar shima yana saka kiransa amma abu daya ne baa daga wayar. Saleem ne ya kalli Daddy mahmoud yace "Daddy bara naje na dubosa tinda dai duka tare muka fito" Juyawa yayi ya fice dakin yayi tsit babe me iya cewa komai Ammar suke jira kaman zuciyoyinsu zasu fada sbd qaguwan yaxo ya dubata dan ganin suke kaman bata numfashi kwata kwata gashi basada yadda ko imanin bawa wasu likitocin daman su dubata da asibiti kawai zasu wuce da ita batareda jiran komaiba. Shi kansa AZIZ din ya kira nasa likitocin suna hanyar isowa shiru yayi yana jiran xuwan nasu yana kallan time akai akai cikin basarwa. Sayd ne dayake bayansa ya dan dago kai ya kalla batareda yace komaiba. Sayd din ficewa yayi yana fidda wayarsa ya sake saka kiran su dr Ashir a karo na ba adadin lattinsu. Saleem a gate ya hangi motar Ammar dan haka ya qarasa da sauri yana kallan Motar da mamaki. Bude masa kofa akai a mutunce da girmamawa ya fito yana kallan yanda securities din duka suke a shirye a position. Motar ya nufa da sauri yana budewa yaga yanda jikin Ammar din ke rawa sosai idanuwansa sunyi jajir. Saurin shiga motar yayi yana ambatar sunansa cikeda tashin hankali da fargaba. Qara jijjiga jikin Ammar din yakeyi kirjinsa na kasa daukan ciwo da radadin da zuciyarsa ke masa take yanayinsa ya rikice a gurin kansa yafara juyawa yana wani irin rawa. Saleem fitowa yayi da sauri ya zagayo ya tura Ammar din seat din gefe ya hau na driver bai tsaya komaiba yayi baya da motar yabar gurin dashi zuwa gida cikin tsananin damuwa da sabon tashin hankalin waye zai duba jannah datake tsananin buqatan taimako a yanzu. Zaadens ya isa dashi wanda sai alokacin Mimi tasan abinda yake faruwa itada Anny dan haka dole Anny tafara basa taimakon gaggawa saleem na taimaka mata Mimi kuwa tashi hankalinta sosai sbd gabaki daya a yanzu cikakkiyar lafiya neman gagarar Ammar din takeyi wanda kuma hakan a cikin kwakwalwansa yakeyi dr ta fada a dena bari yana yawan shiga wannan halin akai akai sbd akwai matsala sosai da hakan. Saleem ne ya buga waya ya sanar dasu Dad abinda ake take hankalinsu ya sake tashi da tsananin tinanin ina mafitar take sbd Ammar dinne kadai likitan da zai duba jannah gashi shikuma ciwonsa ya rasa lokacin tashi sai yanzu wanda suke mamakin menene ya samesa daya haddasa hakan. A daidai wannan lokacin Su dr Ashir suka iso aka bude musu gate suka shigo tareda qarasowa ciki babu bata lokaci suka fara bata taimakon datake buqata shi da dr Sameera da nurse da suka taho da ita bayan kowa ya fice daga dakin. Dayake wannan karan shine zuwansu na farko limbas dan haka palonsa na baqi aka isa dasu suka zauna Maheer na rasa zabin daya wuce yayi contacting Su Abraham sbd akwai yiyuwar dole sai sun taho din tinda Ammar da aka saka ran zaiyi handling situation din basai sun dawoba ya rikice shima dan haka bazai iyaba dole su qaraso su karba idan ba hakan ba babu bata lokaci wasu doctors din zasu san anmata dashen zuciya wanda zaa iya buqatan history na ciwonta abinda bazasu taba bari ko a tsautsayiba wani ya taba gani ba kenan. Sai dare sosai aka samu bugun zuciyarta ya dawo daidai tareda numfashinta amma bata farfadoba har lokacin. Nurse aka bar mata su dr Ashir din suka wuce suma su Dad sai alokacin suka tafi bayan Daddy mahmoud ya nuna sunason tafiya da jannah din acan Zaadens kafin ta warware sai a dawo da ita. Dago idanuwa AZIZ yayi ya xuba masa yana kallansa cikeda rashin ganin girmansa a idanuwansa kafin ya dan dauke idanuwan nasa akansa yana gyara zamansa a natse kafin ya bude baki yace "No zata warware anan din doctors dina zasuji da komai she'll be fine and good" Dad kallansa yayi yana son sake magana ko yayane ya basu ita sedai kuma yasan bata bakinsa da energy dinsa kawai zaiyi amma AZIZ din bazai basu itaba ba kuma dan komaiba sbd ya nuna musu karfinsa akanta yanzu ne. Zuciya ba dadi suka baro limbas din cikin tsakar daren badan rayukansu sun so hakan ba. Suna barin limbas Securities suka rufe gate din gidan gabaki daya babu me sake shiga ko fita sai kuma safe insha Allah. #MAMUH ZAFAFA BIYAR KALBIM 500 mamuhgee A DUNIYATA 500 Huguma AJIYA A DUHU 500 Billyn Abdul KIRJIN ME HANKALI 500 Miss xoxo Pay at 0022419171 AccessBank Maryam sani gummi Shedan biya 09033181070 Or mtn vtu at 09032345899*_KALBIM_* _Mamuhgee_ 74 *UMMU_MAHNOOR LUXURIES* (Best luxuries shop) 08034469681 08135142610 Aslm Alaikm ina kuke masu neman luxuries na kayan alfarmar kece raini? Ina masu son su saka sitirar alfarma ta zamani ta manyan mata masu aji da zaa kalleki kallo daya asan sitirar alfarma e kika saka? Shin kunsan me ake nufi sa kayan asalin yan gayu da nuna gayu? Sitirar Alfarma kikeson sakawa? Sitirar da kike ganin manyan mata da ita? Sitirarda zakiyi gayun sallah dake da yaranki a dauka waje kikaje da kanki kika siyota? To kizo ga damarki ta sameki sbd UMMU_MAHNOOR LUXURIES ta kawo miki sauki har gida, Karkice se masu kudi ke iya siya har kema me yar dama zaki samu naki da saukin kudi kuma best quality da kalar zamani data yan gayu, Nidai Mamuh nace duk wadda ke son a buga gayun sallan bana da ita da 'yayanta to tazo gurin UMMU_MAHNOOR LUXURIES tai siyayyar sallanta harma zuwa gaba dan nasan zakuji dadi da fahimtar abinda nake fada akan kayanta💯💯 Abubuwan da zaki samu a gurinta with the best quality na wayayyun mata masu aji yan gayu sune; Atampopi Laces Shadda Materials Shoes Bags Veils Trolleys Jewellerys Oil perfumes Numbers 08034469681 08135142610 Handles Instagram @ummu_mahnoor_luxuries TikTok username @ummu_mahnoor_luxuries Facebook ummu_mahnoor_luxuries ************** Koda suka isa Zaadens babu wanda zuciyarsa bata cikin damuwa da bacin rai musamman a halinda suka tararda Ammar,Dad jin yayi kaman zai hadiye zuciyarsa sbd tsananin 'daci. Maheer kuwa gabaki daya hankalinsa na kan magana dasu Abraham da daren zaa fara musu shirin tahowa dan rashin zuwansu kaman akwai barazana ga sanin zuciyar wata ce a kirjin jannah dan haka sam shi baya wasa da koman qanqantar hanyar da zata iya kawo musu matsalar sirrin dayake rufe dan haka hankalinsa yake kai yake kuma kan Jannah din da Ammar da dukkaninsu suke mamakin abinda ya samesa. Mimi kwana tai akan Ammar tana hawaye sbd halinda daya kwana a cikinsa wanda takejin kaman sun kasa riqe marayan Allah da baida uwa baida uba tinda uban baitaba nemansa ba a matsayin dansa. Har cikin ranta take tsananin kaunar Ammar fiyeda sauran yayanta sbd irin kauna da tsananin son dayakewa Jannah tin tana ciki hakama dole ta kaunaci jinin Zayneb. Su kansu dad a damuwar suka kwana ta Ammar din da jannah, Kawai abinda ya saka suke jin ta jannah sosai shine hadda sbd sirrin dayake tattare da nata ciwon. Washe gari da sassafe Falaq ta fito ta nufi bedroom din jannah wanda tana isa ta bude kofar kai tsaye ta shiga. Ga mamakinta Daddynta ta tarar zaune a sofa sanye da kayan geamin dinsa da alama daga can din yayo nan din. Fararen idanuwansa ne akan jannah din wadda kallo daya zakai mata zuciyarka ta karye sbd ta qarasa komawa abin tausayi gabaki daya ciwon boye dana bayyana ya bugar da ita a lokaci kankani. Kallanta yake a natse kowace halittar dake fuskanta tana tsayawa a cikin idanuwansa tana shiga kansa... Falaq qarasowa tai zuciyarta na farin cikin ganinsa a dakin gurin jannah wadda ta gama yadda a yanxu bayan Daddynta da Uncle dinta babu wanda take jin tana tsananin kauna kaman Jannah din dan haka bazata qara bari ko daddynta ne ya sake saka jannah din damuwa ba indai tana kusa. Zaunawa tayi ahankali gefensa tareda kama hannunsa tana kallansa ganin yanda yayi relaxing yana kallan Jannah din a natse hotonta abinda ya faru jiya yana tsaye cak cikin kansa na kiran wayar Ammar da daukanta. Idanuwansa falaq din taiwa kallo daya taga yanayin da bata taba ganin Daddyn nata a ciki ba sbd baya taba bari a gane yanayinsa koda ta cikin idanuwansa ne ya qware a boye komai na cikinsa amma a yanxu ba ja sosai idanuwan sukai ba wani tsoro taji data kalla cikinsu ta kwantar da kanta jikinsa da sauri batason kallan cikin nutsuwa tace "Goodmorning Daddy" Rufe idanuwansa yayi Ahankali tareda sauke boyayyar numfashi kafin ya juyo ya kalleta a natse yana kama hannunta dayake cikin nasa ya bude baki cikin kulawa da kaunarta datafi masa komai yace "Morning Falaq Aziz, Yaya?karki saka damuwa a ranki sosai akan nata ciwon,she'll be fine" Kallansa falaq tai ahankali tana jinjina kai kafin ta bude baki tace "Daddy banason komai ya samu My Jan, Batada lafiya,tanada heart problem Daddy" Kallan falaq din yayi da sauri yana mamakin yanda akai ta sani Gyada masa kai tayi tana cigaba da cewa "Yes Daddy,ta fada mun sbd naga yanka a gurin heart dinta inata tambayanta meya jin mata ciwo a gurin so ta fadamun, Daddy tayi fama da ciwon zuciya na shekaru masu yawa tin yarinta, Ta rasa shekarunta na yarinta, Ta rasa childhood nata, Ta taso a boye sbd ciwonta, Ta cire rai daga rayuwa kwata kwata sbd ta kasa samun donor sai a lokacin da time ya qare mata aka samu donor daga wani namiji wanda aka bata zuciyarsa shine Allah ya bata sabuwar rayuwa sbd kwananta be qareba, Daddy jannah nada zuciya me kyau wanda ban saniba ko zuciyar datake kirjin nata ne amma tin daga lokacin data warke haryanxu bata denawa wanda ya bata zuciya addua ba..." Yanda hannuwansa suke rawa sosai yana kokarin hana falaq din ganewa sbd yanayinsa dayake sauyawa matsalansa na neman dawowa ya sakasa miqewa yana kasa iya cigaba da saurara ya bar dakin baya ko gani sosai ya nufi palonsa ya shige ya rufe ya nufi bedroom dinsa wanda yana isa kasa iya cire kayan jikinsa yayi sedai ya yagasu da karfin gaske yana jefarwa ya fada toilet ya sakarwa kansa ruwan dumin da hayaqinsu ke dan fita ahankali suna gauraye toilet din shikuma sosai jikinta ke rawa ya daki bangon toilet din da karfin gaske har saida hannunsa ya fashe amma sam bayajin komai sai masifar dayake ji a cikin kansa da kirjinsa mai tsananin gaske. Jinin dayake zuba a hannunsa ne yake gauraya da ruwan dayake sauka a qasa daga jikinsa suna sauya kala suna gangarawa. A duk lokacinda maganar yanda aka raba Ummitah da ranta ta taso yanayinsa tashi yake wanda duk yanda yake ganin likitocinsa many akan hakan yanayin ya kasa rabuwa dashi lokaci daya duk da ya rage sosai amma yanayi me matiqar hadari yake shiga batareda sanin kowa duk duniya ba bayan Sayd. Trauma din Ammar Zad a bayyane take wanda shi kuma tasa dataci uban ta Ammar din yake a boye sbd yafisa sanin gwagwarmaya da iya taku tareda kwarewa a iya controlling kansa sabanin shi nasa dayake bayyane ga duniya ma kila. Ya dade a ciki kafin ya samu iya controlling kansa yanayinsa ya fara dawowa daidai ya zari towel ya dauro a qugunsa ya fito bayan ya nade hannunsa dayake dan zubar da jini har lokacin ya shirya a natse yana kallan fuskansa cikin mirror zantukan falaq na yawo a cikin kunnuwa da zuciyarsa har lokacin, Menene Jannah din take nufi da zuciyar namiji ne a kirjinta? Boye gaskiar ne takeyi kokuwa iyayen nata da lover boy din nata basu fada mata gaskia ba? Shin kafin komai ma da saninta kuwa suka raba wata da ranta dan bata zuciya? Ta Aminta da a raba mace me tsohon ciki da ranta dan ita ta samu sabuwar rayuwa? Dakatawa yayi daga saka agogon diamond din dayake hannunsa ya zubawa mirror idanuwansa da har lokacin basu qarasa komawa daidaiba abubuwa da yawa ne suke cikinsu suna qonasu. Karfe goma ya fito dauke da wayarsa yana duba tarin misscalls daga Zaadens wanda babu wanda ya gani bare dauka. Su mama dake palo dukkaninsu Qamshinsa ya gauraye palon cikin sanyi ya sakasu kallan hanyar fitowansa Sai gashi ya fito kwarjinsa da kamewansa ta saka su fadilah sauke idanuwansu mama kadai ce bata dauke idanuwanta akansa ba cikin kulawa ta amsa gaisuwansa tana sake tambayar jikin jannah duk da taje ta dubota har so biyu da safen. Fadilah dagowa tayi cikin girmmawa da wayewa ta gaidasa ya amsa batareda ya kalleta ba ya nufi dining. Dukkaninsu yau sukai breakfast kaman yanda suka saba hadda falaq sbd jannah nata farfado ba. Suna gamawa su dr Sameera suka iso shikuma ya fice daga gidan. Yana ficewa Anny da Mimi tareda saleem da maheer da mommy suka iso gidan sukuma. Dukkaninsu babu wanda zuciyarsa bata tabu da yanda suka gantaba da yanda ta koma. Abinda ya dan ragewa Mimi tsananin nauyin da kirjinta yayi shine ganin yanda falaq take kulawa da jannah din sbd koda suka iso ta rage mata kayan jikinta tana goge mata jikinta da lallausan qaramin towel da ruwan dumi sosai ita da Fiddausi. Hadiye hawayenta Mimi tayi sbd duk gwagwarmayansu akan jannah ta qare a inda masu aiki ne da qaramar yarinta ke kulawa da ita tana yashe a daki batareda anbata taimakon datake buqata ba. Ga wanda bai taba mahimmancinta da komai na rayuwarsa ba an cutatar dashi ta hanyar hana masa abinda zuciyarsa ke so ita kadai idan Ammar ya samu ya yadda ya fuskanci kowane irin talauci da ukubar rayuwa idan har jannah na tare dashi. Anny ma sanyi jikinta yayi sbd bata taba dauka jannah zad zata taba dawowa haka ba, Idan har zaa iya daukan rayukan mutane akan jannah to bata taba tinanin zata taba ganin jannah a irin wannan halinba na daukanta batada mahimmanci ko kadan. Suna gidan likitocin da suke dubata suka buqaci zaa koma asibiti da ita sbd acan xaa bincika ciwonta dakyau yanda ya kamata. Kai tsaye Maheer ya nuna rashin Amincewansa da hakan karshe ma ya mama yayi magana da ita da kansa akan suna son tafiya da jannah din sbd tanada likitocinta na musamman da zasu taho dan ita kadai daga wata qasar. Mimi ma baki ta saka suka buqaci Amincewan maman sbd ita kadaice zata amince su tafi da jannah din AZIZ ya dawo baice komaiba. Mama ita kanta batason a tafi da jannah din amma yanda mimi tai mata bayanin yanda yanayin ciwon jannah din yake sai tace saita kira AZIZ ta sanar masa. Kiransa tai yana dauka kai tsaye ta sanar masa tanason ya bari iyayen jannah suje da ita gida likitocin da suka saba dubata su dubata tinda haryanzu bata farfado ba. Shiru yayi batareda yace komaiba tsawom mintina kafin ta sake maimaitawa ya bude baki a taqaice yace "Ba damuwa duk yanda kikace mama amma su tafi zan kaita na kaina amma sai likitocin nata sun sauka qasar ina buqatan ganinsu da kaina" Yana gama fadan hakan ya kashe wayar sbd yasan suna sauraronsa. Mama kallansu tai sbd sunji da kunnensu idan sun aminta da hakan shikenan idan basu aminta ba itama tafiya da jannah bai kwanta mata bare falaq datake jin kaman zatai kuka zuciyarta da jikinta na sanyi. Basada zabin daya wuce amincewa da hakan dan haka suka tattara suka koma da jiran saukar su Abraham da Ken Nigeria sbd tin barin Ken Nigeria ya koma yaron Abraham ya zama baturen kansa shima sbd ya tabbatarda idan ba cigaba yayi da binsu ba zai samu kansa a matakin da dr ismail ya taka sbd duk wanda yake cikin wannan sirrin an dade da rife babinsa iya su yanzu suka rage. Wanna sharadin na AY LIMBA ya saka dole zuwansu Abraham ya dawo a kwana daya dan haka a washe gari ake jiran saukarsu Nigeria. Ammar ya dawo daidai sedai ciwone yanzu me tsananin radadi yake cin zuciyarsa, Kewan mahaifiyarsa yake sosai radadin rashinta na dawo masa, Ya rasa walwalwansa da farin cikinsa gabaki daya bayajin dadin komai na duniyar jin yake inama yabi Amminsa ya huta da abinda yakeji a zuciyarsa da gangar jikinsa. Hoton jannah dayake dakinsa ya qurawa idanuwansa dasuke masa yaji da radadi sunyi jajir ya bude baki zaiyi magana amma baya iya cewa komai sbd tsananin damuwar datake neman taba kansa. Mimi da Saleem suke tsananin jin ciwonsa a cikin ransu suna jin tasu zuciyar na cikewa da nauyi da dacin ganinsa a halin dayake ciki sbd ya dena fitowa kwata kwata, Dad da daddy mahmoud duk yanda suke zaryan zuwa dakinsa sam baya budewa sbd bayason ganin kowannensu sbd idan yana ganinsu Amminsa yake gani a tare dasu dan haka baya son ya tsanesu sbd tsananin kaunar dayake wa Amminsa. #MAMUH ZAFAFA BIYAR KALBIM 500 mamuhgee A DUNIYATA 500 Huguma AJIYA A DUHU 500 Billyn Abdul KIRJIN ME HANKALI 500 Miss xoxo Pay at 0022419171 AccessBank Maryam sani gummi Shedan biya 09033181070 Or mtn vtu at 09032345899*_KALBIM_* _Mamuhgee_ 75 *UMMU_MAHNOOR LUXURIES* (Best luxuries shop) 08034469681 08135142610 Aslm Alaikm ina kuke masu neman luxuries na kayan alfarmar kece raini? Ina masu son su saka sitirar alfarma ta zamani ta manyan mata masu aji da zaa kalleki kallo daya asan sitirar alfarma e kika saka? Shin kunsan me ake nufi sa kayan asalin yan gayu da nuna gayu? Sitirar Alfarma kikeson sakawa? Sitirar da kike ganin manyan mata da ita? Sitirarda zakiyi gayun sallah dake da yaranki a dauka waje kikaje da kanki kika siyota? To kizo ga damarki ta sameki sbd UMMU_MAHNOOR LUXURIES ta kawo miki sauki har gida, Karkice se masu kudi ke iya siya har kema me yar dama zaki samu naki da saukin kudi kuma best quality da kalar zamani data yan gayu, Nidai Mamuh nace duk wadda ke son a buga gayun sallan bana da ita da 'yayanta to tazo gurin UMMU_MAHNOOR LUXURIES tai siyayyar sallanta harma zuwa gaba dan nasan zakuji dadi da fahimtar abinda nake fada akan kayanta💯💯 Abubuwan da zaki samu a gurinta with the best quality na wayayyun mata masu aji yan gayu sune; Atampopi Laces Shadda Materials Shoes Bags Veils Trolleys Jewellerys Oil perfumes Numbers 08034469681 08135142610 Handles Instagram @ummu_mahnoor_luxuries TikTok username @ummu_mahnoor_luxuries Facebook ummu_mahnoor_luxuries *********** Sai dare ya dawo gida shi kadai sbd Sayd yana jos acan zai kwana yaje karbo duk wasu takardu da records na Asibitin Zaadens daya boye bayan wanda suka tabbatarda sun karbe daga hannunsa sbd AZIZ da kansa yayi magana da Matar ismail din sbd ya bayyanar mata da kansa tareda sanar da ita komai dan haka da kanta ta kusa cikin kayan Dr ismail ta samo musu duk wani abi da zai dan taimaka musu ciki kuwa hadda date na ranar aikin da time da akai aikin da record din Ummitah na komai da sukai mata tin a asibitin dr ken tareda copies na transactions da akai musu shi da dr ken da tarin kudaden da suka ringa basu masu yawan gaske. Koda ya iso gida kusan duka kowa ya shige dan haka kai tsaye Bedroom dinsa ya nufa yayi wanka ya sauya kaya zuwa na bacci masu dan kauri ya fito sanye da slippers a kafafunta. A kaidar aikin Fiddausi indai yana gari to ko karfe nawa zekai bai dawoba zata jira dawowansa sbd gabatar masa da abinci kokuma tea ko wani abinda zai buqata na ci nara nauyi. Dan haka ko yanxu ma batai bacci ba suna dakin Jannah itada falaq datai bacci a zaune sbd tsaron jannah,ita kuma tana kokarin goge mata jikinta da son sauya mata kaya taji anbude kofar dakin kai tsaye a natse. Juyowa Fiddausi tayi a natse taga shine take ta ajiye rigar jannah din data zare tana miqewa tsaye da girmamawa tai masa sannu da zuwa. Falaq ya kalla cikeda tausayawa yaga yanda itama ta fada kafin ya maida kallansa akan jannah wadda take qara ramewa da sauyawa sosai a kwancen. Numfashi mara sauti yasauke kafin ya tako a hankali ya rankwafa ya dauki falaq gabaki dayanta ya juya ya fice da ita xuwa dakinta ya kwantar da ita ya rufeta da abin rufa yayi mata addua ya kashe wuta tareda daidaita mata ac ya fito ya rufeta ya koma dakin jannah din. Koda ya isa Fiddausi ta sauya mata riga mara nauyi tana kokarin fara goge mata jikinta. Tana ganinsa ta ajiye ahankali tareda ficewa daga dakin gabaki daya ta nufi kitchen ta hado masa lemon tea da sabon cake da aka gasa yau na chocolate sai dabino da madara me dumi ko zai saka a tea din tana ajiyewa ta juya ta fice tareda jan kofar dakin. Zubawa jannah din idanuwansa yayi tsawon mintina kafin ya zauna ahankali tareda miqa hannunsa ya dauki towel din da baa warwareba ya warware ya saka a cikin ruwan zafin masu tsafta sosai da Fiddausin ta ajiye. Ahankali ya rage ruwan towel din sosai kafin ya yaye rufar datake jikinta ahankali ya dora towel din da hannunsa a fuskanta yana gogewa. Cikin nutsuwa da mamakin kansa yake goge mata fuskan harya kammala da fuskan ya gangaro wuyanta ahankali yafara gogewa a natse. Yana kawowa kirjinta kasa wucewa gaba yayi ya tsaya cak a gurin yana saukar da idanuwansa akan aikin zuciyarta yana jin zuciyarsa na sanyi jikinsa na dumi damuwa da tausayin kansa daya rasa macen dayafi kauna fiyeda komai a duniyarsa, Ta tafi bazata taba dawowa ba har abada,ta tafi tabarsa da tabo da ciwon da bazai taba warkewaba na rashinta, Kaunar Ummitah halitta ce da Allah ya halitta masa a cikin zuciya da jininsa, Ummitah rayuwarsa ce,ruhinsa ce,jinsa da ganinsa ce, Ummitah itace asalin ABDULAZIZ AYOUB LIMBA ayau daya rasata gabaki daya ya rasa kansa sbd gashinan ya koma tamkar me ciwon haukar juyewan kwakwalwa a boye, Ya rasa wani bangare na rayuwarsa da har abada bazai taba dawowa ABDULAZIZ dinsa na asali ba sbd rashin Ummitah, Kaman yanda take kallansa a matsayin uwa da ubanta da kuma hammanta a garesa shima Ummitah itace uwa da ubansa daya rasa da kuma 'ya da kanwarsa gaba daya itace familynsa datake dauke da matsayin kowa da family ke buqata ya cika. Wasu hawaye masu tsananin zafin da baisan da su bane suka gangaro suka sauka akan fuskan jannah wadda idanuwanta suka bude tsowon seconds goma da suka wuce. Idanuwanta da basa gani sosai sbd ciwo da dadewa a kwance ta zuba masa batareda ta iya motsa komai na jikinta, Bata ganinsa sosai amma dai tasan shi dinne dan haka zuciyarta tai wani irin sanyi cikin damuwa da ciwo hawaye masu zafi sika gangaro da gefen Idanuwanta. Hannunsa ya motsa ahankali ya dora akan zuciyarta dake bugawa cikin sanyi ahankali da nutsuwa tareda wani irin tsananin sonsa datake jin kaman illa ne ma gareta zuwa yanzu sbd ya gama tabbatar mata da bazai taba sonta ba har abada. Shiru sukai kowannensu idanuwansu jajir da radadin da zuciyoyinsu suke ciki, Bugun zuciyarta yake sauraro da tafin hannuwansa yana isa ga tasa zuciyar yana jin kaman ya ambace ta da sunan Ummitah ta amsa masa ko zai samu abinda yakeji a kirjinsa na shekaru ya dan fada masa ko zai iya dawowa cikakke lafiyayyan mutum daya rasa lafiya da cikakken hankalinsa.... Itama nata idanuwan har lokacin gangaro da hawaye masu ciwo da zafi sukeyi batareda ta motsaba dumin tafin hannunsa dake kan zuciyarta yana isa cikin zuciyarta yana qarasa mata illar da har abada tasani bazata taba iya dena sonsa ba sbd jinsa takeyi har acikin jininta ba iya zuciyarta ba, Batasan wane iri so bane wannan wanda yake sakar mata ciwo da radadi ta kasa ciresa a ranta, Bazata iyaba duk yanda taso hakan sbd son nasa yai mata mummunan illar da ita tata rayuwar ma ta gama mutuwa akansa, dan haka rufe idanuwanta tayi ahankali tana jin inama ta tafiyarta itama ta huta da wannan radadi da ciwon datake ji kila shima zai samu nutsuwar zuciya idan ta tafiyarta tabar masa duniyar. Ahaka suka raba dare sosai har saida ta motsa kadan ta bude idanuwanta a wahalce sai alokacin ya dago ya kalleta yaga idanuwanta a bude sunyi jajir da hawayen dataita yi tin dazun. Hawayen dake gangarowa daga idanuwanta yabi da kallo yana yana dauke hannunsa daga kirjinta tareda xare hannunsa daya dayake cikin nata ya juya ya fice baice komaiba ta bisa da kallo. Nurse din dasuka dauka ne ya turo mata ita ta dauketa takaita toilet tayi fitsari ta gyaro mata jikinta daqyar sbd babu abinda yake motsi a jikin jannah din bata iya motsa komai nata. Washe gari tinda safe dr Sameera ta iso gidan koda ta iso yana babban palo zaune tareda mama da sai Fiddausi dake kai da kawon aikin hada dining. Falaq kuwa farin cikin ganin jannah ta farfado ya saka tinda safen ta saka Nurse tai mata wanka aka saka mata riga da wandon jeans marasa nauyi aka turota a kujera jannah dince ta turota suka fito palo jannah din batada karfi ko kadan magana ma bata iyayi bare iya motsawa sai an taimaka mata a komai. Dr Sameera kuwa hannun AZIZ din da dr Ashir yayi dressing jiya taxo dubawa dan warwarewa ta duba ciki. Cikin kulawa ta kallesa bayan sun gama gaisawa da mama a sake ta sake kallansa cikin kulawa tace "Hannun zan duba naga idan zaa sauya bandage dinne" Mama kallan hannun tayi tana cewa "Yarsa ce bata lura da hannun ba da yanxu ta daga mana hankali ai" Murmushi dr Sameera tayi yana miqa hannunta akan hannunsa daya dora mata akan Hannun sofan dayake zaune batareda ya kalletaba yana duba abu a waya. Nurse ce ta kawowa Sameera akwatin first aid ta kama hannunsa a hankali zata fara warware bandage din su falaq suka shigo palon da jannah wadda idanuwanta da sukai laushi sosai sbd ciwo suka sauka akan hannunsa da dr Sameera ta riqe da sunan dubawa. Tsayawa falaq tai tana kallan dr Sameera din zuciyarta ba dadi. Jin shiru ya sakasa dagowa ahankali idanuwansa akan Jannah data dauke idanuwanta ahankali akan hannuwan nasu suka fara sauka ya zare hannunsa daga gyaran yana cewa ba buqatan wani bandage din abar masa hannun haka. Falaq kuwa qarasowa tai gurinsa da sauri tana kama hannunsa da kulawa tana cewa meya samesa. Mama kuwa jannah ta tashi ta qarasa turowa har gefenta tana mata sannu da ido kawai jannah ta iya amsawa zuciyarta ba dadi ko kadan sbd ta riga da ta rasa farin cikinta rayuwarta ta sauya daga jannah zad a yanxu batasan ita wace jannah dince ba. Bata iya sake kallan inda kowa yakeba rufe idanuwanta tai tana sake zama weak yana lura da yanayinta dan haka da kansa ya maidata daki batareda kowannensu yayiwa kowa magana ba ita a yanzu kallansa ma batason yi sbd shine yake qara azabtar da zuciyarta dan haka ta hakura ta bawa zuciyarta salamar hakura da wanda baya kaunar komai daya shafeta. Yana ficewa wasu hawaye masu dumi suka gangaro mata ta rufe idanuwanta tana tsananin son ganinta cikin familynta dake tsananin buqatanta a lafiya da ciwo. Shi kansa zuciyarsa daci take masa dan haka ko abincin kirki baiciba yace Fiddausi ta hada kayan jannah din a luggage qarama. Sayd ne ya iso shima a lokacin latif ya daukosa daga airport dan haka tin kafin ya iso gida a waya ya sanar dashi ABRAHAM da KEN sun sauka a abuja Nigeria dan haka ya saka Fiddausin hada kayan jannah. Da kansa ya daukota tin daga cikin dakinta a hannunsa ya fito da ita xuwa mota da Sayd ya shirya musu. Da falaq aka tafi dan haka dashi da ita jannah dinne a bayan motar sai falaq a gaba Sayd na tuqa motar suka nufa zaadens baida niyar barinta acan din amma sbd umarnin mama ne kadai zai kaita kuma a gobe zai dawo da ita limbas. Suna isa limbas gabaki daya familyn jiran isowansu akeyi sbd sunta kira su sanar masa isowan likitocinta amma sam babu wayar wanda ya dauka sedai suka kira Sayd suka sanar masa wanda yana sane da saukar su Abraham din sbd sun saka tsaro sosai akan isowansu. Ammar da Mimi take riqe da hannunsa sbd yanda yake kasa riqe zuciyarsa akan jannah dago jajayen idanuwansa yayi yana kallan yanda AZIZ LIMBA yake dauke da jannah a gaban idanuwansa ya wuce da ita ciki ta gabansa ita kuma idanuwanta suna kansa tana masa kallan mamaki da bankwana sbd batajin zata iya komawa gidansa ta hakura da auren sbd zuciyarta bazata iya daukan kallan qinta a cikin idanuwansa ba da kuma yanda tsananin sonsa dayake bayyane a idanuwan Fadilah da dr Sameera dan haka ta zabi dawowa hannun familynta ta qarasa mutuwarta a hannunsu idanma ciwon bame barinta bane kenan. Har bedroom palonta dayake hade da lafiyayyan bedroom dinta yakaita ya ajiyeta ahankali ta tsaya da kafafunta tana kallansa shima ita ya kalla da idanuwansa dake bayyanar mata da wani tsananin zafin hoton da idanuwanta suka sauka akai na Ammar hakama Ammar dinne duk yanda Mimi taso hanasa isa ga jannah din ya kasa riqe kansa dan haka akan idanuwan AZIZ Ammar din ya shigo palon idanuwansa akan jannah zuciyarsa na samun sassaucin azabar dayake ciki.. Wani kallo Daya saka jannah jin idanuwanta sun ciko da hawaye yayi mata ya bude baki tsananin dayake cikin idanuwansa baya boyuwa zaiyi magana ya fasa sbd zai iya loosing control dan haka Ammar din ya juyo ya kalla ya bude baki yana controlling kansa sbd hannuwansa da suka fara wani irin rawa idanuwansa na sauyawa yace "Ka tabbatarda wannan kallan shine na karshe akan matar da aurena yake akanta sbd nxt kallo da zakai mata irin wannan shine ganinka na karshe sbd saina tabbatarda an saka maka da dabobbi" Dad ya kalla yace "Idan aka take mutuncin igoyiyina wannan shine zuwanta na karshe har abada" Tsit sukai babu wanda ya iya cewa komai sbd rasa abin fada, Mimi gurin Ammar da hannuwansa ke rawa sosai ta nufa da sauri idanuwansa na cikowa da hawaye masu tsananin ciwo. Jannah kuwa tinda AZIZ din ya fara magana idanuwanta suka sauka akan hannuwansa dake wata irin rawa batareda kowa ya lura da hakanba, Wani abu taji yana danne zuciyarta me tsananin nauyi da ciwo, A iya saninta datake dashi tasan me wane ciwo ne yake samun irin wannan yanayin sbd akan Ammar ta fara sanin hakan, A idanuwansa ta maida nata idanuwan tana kallan yanda suka sauya hannuwansa na tsananta rawa yana kokarin controlling kansa. Jin tayi ta kasa riqe zuciyarta daga azababbiyar soyayyarsa data rufe mata ido har ta bari ya tafi a hakan bazaiyi nisa ba zai iya loosing control na kansa kowa ya san halinda yakeji cewan yana tattare da masifaffiyar trauma shima hakama idan har wannan shine haduwarsu ta karshe data yankewa kanta tana fatar ta kasancewa abinda zata ringa tinawa da ita dashi har abada dan haka ko taku biyu baiyiba ta tattaro karfi a jikinta ta riqosa. Su dad na ganin hakan shi yafara juyawa ya fice.... AZIZ kuwa dayake gap da rasa control da zafin gaske ya juyo idanuwansa jajir sedai ba zato ta kamo wuyan rigarsa ta ta hade bakinta d nasa cikin wata irin nutsuwa. #MAMUH ZAFAFA BIYAR KALBIM 500 mamuhgee A DUNIYATA 500 Huguma AJIYA A DUHU 500 Billyn Abdul KIRJIN ME HANKALI 500 Miss xoxo Pay at 0022419171 AccessBank Maryam sani gummi Shedan biya 09033181070 Or mtn vtu at 09032345899*_Arewabooks@Mamuhgee_* 76 *ZUZEAM VENTURES* Best APHRODISIAC 08144015291 Aslm barkanmu da wannan lokaci Ina Mai farin cikin sanar daku cewa Zuzeam ventures takawo maku ingantattun magunguna masu inganci cikin Aminci Muna da kaya kamar haka Mallaka Maganin sanyi Maganin cire tumbiMaganin farin jini Maganin matsiMaganin mata Maganin sa ni’ima da dandano Dulka Amare Set na gyran jiki Set na amarya Tabaje tsumin Gomba Xuma kiba ta hips and Brest Magungunan gyran Brest Magungunan Karin hips Maganin sliming Muna da kaya masu inganci cikin sauki da rahusa Ina wadda keneman mallaka sahihiya quaranty wlh hajiya kixo ga zuzeam ventures xakiji ddin mallaka duk fadin ran ogah duk fadansa wlh sai yyi sanyi 08144015291 Idan maganin mata kikeso akwai Idan gyran jiki kikeso gyran fata gyran Brest magungunan sa kiba da hips DOMIN samunta Kai tsaye kira wannan no 08144015291 DOMIN mgn da ita whatapp 08144015291muna tura kayanmu ko ina cikin iKon allah 🥰👌🏻 Bononza Bononza Tsimin mangoro 1k🥭 Tsimin dabino 1k Gumba ukku balai 700 Gumba aya da nonon rakumi 700 Garin kafi ciccibi 500 Garin bata gaban kishiya 500 Matsin mallaka tada zaune tsaye 2500 Turaren mallaka ba aba mai kishiya 2500 Total kayan 9500 Za a bakisu akan 3800 Kuma mutun goman farko nadakyautar Abun 2k 🗣️🗣️🗣️🗣️🗣️🗣️ ASSALAMU ALAIKUM ALHAMDULILLAH YAN UWA NEW PROMO YA KAMMALA💃🏽💃🏽💃🏽😁😁😁 da 5k dinki ki kwashi kayan 12k hajiyata 💃🏽💃🏽💃🏽😃🙃Kazar gadali ta mallara Rabi 3500 Tsimin gam gam 1500 Ruwan kara zunzurutun dadı😋800 Garin 7in1 1k Gumba 3 balai 500 Gumba kwakwa da dabino 500 Infection ruwan tsarki 1k Garin zunzurutun dadi 1200 Matsin ba a fira d wando 500 Matsin infection mai matse mace gam 500 12k All at 5k kedai dannan link dinnan don samun naki ki maza kiyi bucking koda kudinki saida Rabonki ************* A cikin tsakiyar bakinsa bakinta ya isa direct dumin bakinsu yana haduwa da juna abinda bai taba faruwa dasu su dukanba, Bai tinda yake bayan kumatu da goshin da hannuwan falaq dayake wa pecks lips dinsa basu taba haduwa da fatar kowaba dan haka shock din dayake ciki ya ninku sbd dumin bakinta daya shiga cikin nasa da kyau yana tayar da duk wata tsigar jikinsa hannuwansa na tsananta rawa ya daga zai janyeta daga jikinsa, Yana dago hannun ta saka nata tafin hannun a cikin nasa ta riqe hannunsa tana kissing tsakiyar bakinsa da kyau cikin nutsuwa da sanyin daya kashe dukkanin jikinsa wutar ciwonsa na mutuwa sedai tana mutuwa ne da wani sabon masifaffen zafi da tiriri jikin daya sakasa mata wani mugun riqon daya kusan karya qugunta ta bude idanuwanta ta zuba masa ahankali shima ita din yake kalla da idanuwansa da sukai mugun ja..... Ammar dayake tsaye kasa daukansa kafafunsa sukai wani mummunan jiri ya dibesa Mimi data kasa juyowa sbd yanda zuciyarta ke quna itama hannunsa take kokarin ja ta fice dashi amma sam kafafunsa sun mutu sai jin tayi ya zube a gurin.... Maheer ma da Anny ficewa sukai tin farkon lokacinda Jannah ta kamo LIMBAn, Mimi ma bata tsaya ganin abinda zai faruba ta juya amma batareda ta saki hannun Ammar ba datake jansa su fice dan haka batasan meya gani ba amma zuciyarta suya take mata saida taji zubewansa ta juyo har lokacin bata kalli inda jannah da AZIZ din sukeba. Falaq ce ta shigo kai tsaye itama da saurinta sbd ganin kowa na fitowa fuska ba dadi. Akan Daddynta dayake riqe da jannah din datake riqe da kwalar rigarsa har lokacin idanuwanta suka sauka da sauri ta juya tana jin kaman farin ciki yana rufeta me tsanani. Sayd ta kira da sauri tace yaje ya fiddowa da Mimi Ammar zad daga palon, Jin hakan ya saka Maheer da Saleem nufar palon cikin tashin hankalin jin Ammar ya zube. Shigowansu ya saka Jannah din zare bakinta daga nasa ahankali tana zare tafin hannunta dayake hade da nasa tana kallan fuskansa datai ja gabaki dayanta musamman dogon hancinsa da shima yayi jajir. Kugunta da yayiwa mugun riqon daya kusan ballata ta dan janye tana jin kaman bazata iya tsayuwa ba tai kasa da kanta tana juyawa sbd jin bazata iya jurewa kallansa ba da idanuwansa dake neman zarar da ita.... Shi kansa jin yayi dakin yana juyawa dashi sosai hakama wani mummunan zafin dabai taba ji ba yaji yana rufesa tin daga kansa har zuwa qafafunsa dan haka bai kallo kowaba ya juya ya fice hannuwansa na dan dawowa da rawarsu sedai dumin dayake tafasa jikinsa yafi karfin rawar hannuwan. Yana fitowa falaq taji wani irin faduwar gaban ganinsa sbd bata taba ganinsa a hakanba, Hannunsa ta kama da sauri suna nufar kofar batareda tace komaiba, Sayd ma yana ganin yanayinsa yayi saurin bude masa mota suka shiga yaja motar suka bar gidan da wani irin speed. A motar wani irin kokari da karfin hali yakeyi sbd kada falaq ta gane mummunan yanayinsa wanda yau gabaki daya lamarin yafi na koyaushe yakeji sbd duk inda ruwa da jini suke yawo a jikinsa dumi yaji suna dauka tareda tayar da tsikar jikinsa yana rasa ta ina masifar ke bullowa. Sayd kuwa gudu yake cikin kwarewa sbd su isa kan lokaci batareda kowa a motar yayi magana ba itama falaq ta gane Daddynta na cikin wani halin da baya buqatan magana shiyasa tayi shiru tana qanqame hannunsa da sigar rarrashi. Suna isa gida Sayd na pakin Latif dake harabar gidan da gudun gaske ya iso budewa AZIZ din mota cikin girmmawa sedai kallo daya yayi masa ya sauke kai sbd ganin kaman ransa a tsananin bacen da basu taba gani ba. Ciki nufa kai tsaye zuwa bangarensa, Koda ya shigo main Living room na gidan su Mama na zaune suna fira amma babu wanda ya iya ko kalla ya wuce ciki. Yana isa palonsa tin a kofa yafara zare rigarsa ya nufi bedroom ya fada toilet ya sakarwa kansa ruwa da sauran kayan jikinsa. Sayd ne ya samesa har bathroom din dauke da Maganinsa da ruwa ya basa ya karba ya shanye yana rufe idanuwansa ahankali. Ficewa Sayd yayi yabarsa tsawon mintina ya samu dawowa daidai ya fito sanye da bathrobe fara kal ya zauna kan kujeran gaban dresser yana zubawa fuskansa idanuwa, Gangaro da idanuwansa yayi akan lips dinsa da suka sauya kala, Kasa motsawa yayi tsawon lokaci kafin ya rintse idanuwansa ya bude yana jin tsanar kansa kawai, Tsanar zuciyarsa yaji yanayi sosai da sosai sbd ta cutatar da kaunar dayakewa Ummitansa, Zuciyarsa ta zama tamkar maqiyiyarsa a yanzu data bawa kanta damar karban feelings din dabai kamata ba, Tayaya zai iya bari zuciyarsa tayi wannan gagarumin lefin na budewa batareda sani ko ankararsaba, Tayaya wani yanayin daba na fishi da zafi da tsana da qiyayya ba zai samu qanqanuwar dama? Rintse idanuwansa yayi da suka sauya take yana jin tsanar kansa da gasken gaske, Zaiyi yaqi da zuciyarsa da gasken gaske bazai taba barin kowane irin yanayi ya shigesa ba koda hakan na nufin illata kansa ne, Bazai taba bawa Zaadens damaba, Bazai taba barin kowane irin yanayi ya shiga tsakaninsa da tsananin tsanarsu da qinsu da suka riga suka zaune a ransa ba dan haka zai tabbatarda yayi abinda yake gabansa ya raba kansa da duk wani abu dazai sake tina masa su har abada. *******A zadeens kuwa wata irin jijjiga Ammar keyi kaman wanda ya samu ciwon jijjiga, Zuciyarsa ce ke neman kasawa dan haka cikin gaggawa Maheer ne ya daukesa suka fito dashi zuwa Dakinsa Anny na kokarin hada masa taimakon gaggawa duk da wannan karan gabaki daya basu taba ganinsa a mummunan hali irin wannan ba, Dad dayake jin jininsa ya gama hayewa sama da kansa ya ciro wayarsa ya kira Abraham yace cikin gaggawa su qaraso Zaadens kawai. Suna jin hakan driver ya juyo zuwa zaadens dasu batareda sun isa masaukinsu ba. Jannah gabaki daya jin tayi ta qarasa rasa kuzarinta jikinta yayi sanyi sbd zuciyarta tagama mutuwa akan inda bai kamataba, Zuciyarta ce ke juyata batada tinanin kanta ko hankalin kanta sai abinda zuciyarta take sakata, Son AZIZ LIMBA kaddara ce da jarabawa me girman gaske da Allah ya kaddaro mata wadda batasan tayaya zata iya yakice ta daga ranta ba, Ayau idan ba karya idanuwa da zuciyarta suka gano mata ba tsananin kishint ne ta hango a idanuwansa wutarsu na ci, Kishi ne mai zafi da karfin gaske da bata taba ganin irinsa a idanuwan Ammar ba, A irin wannan yanayin ne kuma ta hango trauma me kargin gaske a tattare dashi da zata iya cewa zai iya komai a lokacin sbd fita hayyaci, Hope taji tasamu akan soyayyarta da batada tabbas, Jin tayi a daidai wannan lokacin zata iya cigaba da jure komai akansa, Jin tayi zata iya kasancewa dashi har karshen rayuwarta sbd basa kulawa da kariya a duk lokacinda yanayinsa zai iya motsawa wanda ta tabbatarda duniya batasan dashiba kaman yanda na Ammar dinsu yake kusan a bayyane. A yanxu kuma da idanuwanta suka sauka akan mummunan yanayin da Ammar yake ciki jin tayi ta tsani kanta gabaki daya sbd bataiwa soyayyar da suka taso a cikinta adalciba, Ammar shine yaya mafi soyuwa aranta da ko babu aure zai iya komai akanta kaman yanda yakamata ta kula dashi fiyeda kowa a familynta... Isowan Dr Abraham ya saka aka fara basa taimakon gaggawa wanda ya saka hankalinsu sake mugun tashi sbd jikinsa baya karban kowane taimakon da ake kokarin bawa zuciyarsa dake neman dena bugawa. Cikin damuwa Dr Abraham yace dole ayi gaggawar zuwa asibiti dashi. Basuda zabi dole aka daukesa suka kwasa cikon matsanancin tashin hankali aka nufi asibiti dashi. Ana isa dashi kai tsaye bangaren masu asibitin aka nufa dashi take likitoci dasu dr Abraham din aka rufa akansa. Mimi tayi kuka har idanuwanta sun gaji dan haka suka zubawa sarautar Allah ido suna jiran tsammani, Gabaki dayansu suke asibitin banda jannah da bazata iya fita koinaba sbd ita kanta a yanzu tsanar kanta takeyi sbd tana tsakiyar da batasan me takeso ba. Daddy mahmoud gida aka koma dashi sbd zuciyarsa dake masa ciwo shima sbd sai yanzu yake jin kansa cikin tsananin nadama da baqin cikin abinda akaiwa 'dan zayneb, Sbd girma da tsananin kaunar da sukewa zayneb ne jannah ta samu kaunar me girman da suke mata a yanxu wanda Ammar ne ya bata wannan kaunar wadda shi ya kamata suwa, Shine wanda sukewa kaunar zayneb bayan barinta duniya sedai kuma irin tsananin kauna da kwallafa rai da yayi akan jannah tinda ta fado duniya ya saka suke mata kaunar datake a cikinta ayanzu amma a lokaci daya son zuciya da makancewa ya sakasu sakasa a wannan mummunan halin dayake a ciki yanzu a lokacin daya kamata su tsaya su hana ko waye tabasa. Dad ma tsananin damuwa da baqin cikin hukuncinsu ne y saka nasa hawan jinin tashi anan asibitin shima aka shiga basa taimakon sbd sosai jininsa ya hau din. Har dare kwata kwata baa samu sauki a lamarin Ammar ba wanda duk rashin imaninka kallo daya zakai masa ya baka tsananin tausayi sbd ciwo dai ya sauyasa a lokaci daya. Kaf ahalin zaadens babu wanda baya cikin damuwa me tsananin gaske da tausayin Ammar din, Jannah kanta datake gida tayi kuka mai tsananin gaske tana jin inama rayuwarsu ta baya familyn ta dawo a lokacin da suke tsananin kaunar juna basa cikin matsala ko damuwar komai ta duniya. A asibiti gabaki dayansu familyn suka kwana banda daddy mahmoud da jannah dake fama da kansu a gida. #MAMUH ZAFAFA BIYAR KALBIM 500 mamuhgee A DUNIYATA 500 Huguma AJIYA A DUHU 500 Billyn Abdul KIRJIN ME HANKALI 500 Miss xoxo Pay at 0022419171 AccessBank Maryam sani gummi Shedan biya 09033181070 Or mtn vtu at 09032345899*_KALBIM_* _Mamuhgee_ 77 *UMMU_MAHNOOR LUXURIES* (Best luxuries shop) 08034469681 08135142610 Aslm Alaikm ina kuke masu neman luxuries na kayan alfarmar kece raini? Ina masu son su saka sitirar alfarma ta zamani ta manyan mata masu aji da zaa kalleki kallo daya asan sitirar alfarma e kika saka? Shin kunsan me ake nufi sa kayan asalin yan gayu da nuna gayu? Sitirar Alfarma kikeson sakawa? Sitirar da kike ganin manyan mata da ita? Sitirarda zakiyi gayun sallah dake da yaranki a dauka waje kikaje da kanki kika siyota? To kizo ga damarki ta sameki sbd UMMU_MAHNOOR LUXURIES ta kawo miki sauki har gida, Karkice se masu kudi ke iya siya har kema me yar dama zaki samu naki da saukin kudi kuma best quality da kalar zamani data yan gayu, Nidai Mamuh nace duk wadda ke son a buga gayun sallan bana da ita da 'yayanta to tazo gurin UMMU_MAHNOOR LUXURIES tai siyayyar sallanta harma zuwa gaba dan nasan zakuji dadi da fahimtar abinda nake fada akan kayanta💯💯 Abubuwan da zaki samu a gurinta with the best quality na wayayyun mata masu aji yan gayu sune; Atampopi Laces Shadda Materials Shoes Bags Veils Trolleys Jewellerys Oil perfumes Numbers 08034469681 08135142610 Handles Instagram @ummu_mahnoor_luxuries TikTok username @ummu_mahnoor_luxuries Facebook ummu_mahnoor_luxuries ************ Wash gari dole Dad gado aka basa a asibitin sbd Bp dinsa kwata kwata yaqi dawowa daidai. Mimi ma taqi yadda ko kadan ta baro asibitin itada Saleem wanda Ammar yake cikin ransa sosai dan haka dole Maheer shima ya kasa baro asibitin. Karfe 11 na rana Sayd y iso asibitin sanye d face mask da fcap daukan Jannah wadda tinda sassafe ta iso asibitin ko tsayuwa bata iya yi da kujera aka kawota. Sayd na shigowa dakin Ammar na farfadowa dan jannah ta kalli Sayd din tace yabarta zata dawo daga baya. Baice komaib wayarsa ya fidda ya saka kiran LIMBA yana dauka ya bata wayar yana juyawa ya fice daga dakin yabarta tayi magana dashi idan ya Yadda. Harta yanke bai dagaba dan haka ta ajiye wayar akan kafafunta tana kallan Ammar wanda idanuwansa dake a jeme suka sauka akan hoton dayake kan wayar sayd baro baro na Ummitah da AZIZ wanda asalin kamanninsu suka bayyana kaman an tsaga kara tana dariya a jikinsa. Duk da baya gani sosai rawa hannuwansa suka fara yi yana son nuna hoton Ummitah dayake cikin wayar wadda sukeda hotonta haryanzu a cikin file na jannah. Rikicewa gabaki daya yayi yana wani irin yunkurin magana hannuwansa da bakinsa na rawa. Sayd ne ya shigo dakin ya karbi wayarsa yana barin asibitin da jannah ya maidata gida sbd itama neman rikicewa jikinta keyi sbd tashin hankalin ganin yanayin Ammar. Da gudu likitoci sukayo dakin tareda su Mimi dasu Maheer dasuka je dakin dad dubosa. Suna shigowa Ammar ya damqe maheer da karfin gaske yana kallansa yana kallan Abraham muryansa n sarkew yace "AZIZ limba da donor dinmu, Zuciyar dayake bugawa a zuciyar Jannah AZIZ LIMBA,AZIZ LIMBA ya..... Ganin yana neman fallasa komai a gaban mutane da sauran likitocin batareda yasan me yake fada ba ya saka hankalinsu gabaki daya tashi cikim mugun faduwar gaba da shiga Rikitaccen yanayi dr Abraham ya masa allurar data sakasa zubewa a gurin yana tinanin kwakwalwan Ammar tabbas ta tabu. Anny jin tayi zufa ya rufeta hankalinta na neman tashi da abinda yake shirin faruwa idan baa nema maganin ciwon Ammar da gaggawaba zai iya tona asiri su shiga masifar da babu fita. AZIZ LIMBA karfe 7 na dare motarsa ta isa Zaadens tareda Sayd wanda suke shirye tsaf dan gama komai su tattara su koma inda suka fito. Babu kowa kaf a mansion din sai masu aiki da securities sai Daddy mahmoud daya fito jin isowansu sbd matarsa mummy tayi asibiti da daren dubo Ammar da kaiwa su Mimi abinci masu tarin yawa kala kala. Kasancewan Daddy mahmoud din shima yanada weak heart ya saka abu kadan yake sakasa samun attack ko bugawan zuciya shiyasa ko farkon samun matsalar financial crisis dinsu ya kamu da paralys dakyar ya dawo daidai dan hakanne tin jiya yake fama da ciwon kirji. A yanayinda ya fito yana kallansu ya saka AZIZ masa kallo daya ya hango zuciyarsa gap take da bugawa dan haka fasa zama yayi ya kalli Say wanda yayi amfani da sabuwar waya ya tura sako zuwa wayar Anny. Kallan Daddy mahmoud din AZIZ yai a qasqance kafin ya bude baki yace "Ka dena daga hankalinka akan Ammar Zaaden sbd ya riga ya rasu......... Wani mummunan bugawa zuciyar daddyn tayi ya dago da sauri yana kallan AZIZ hannuwansa na rawa da kafafunsa ya bude baki zaiyi magana AZIZ din ya katsesa da cewa "Tinda wuri zaka buga zuciyarka bayan baka gama jin abinda zan fada maka ba" Girgiza kai daddy mahmoud yayi yana dafe kirjinsa muryansa na rawa yace "Ammar ya rasu?? "Ba shi kadai ya rasu ba hadda Dan uwanka shima lokacinsa yayi na...... Faduwa Daddy mahmoud yayi yana dafe kirjinsa da karfi zuciyarsa na kokarin bugawa ganinsa na daukewa yana son yayi magana amma ya kasa azababbiyar azaba kirjinsa ke masa.... Durqusawa gabansa AZIZ yayi shima hannuwansa na dan rawa idanuwansa n sauyawa zuwa jajir yace "Kirjinka baya iya dauka ko? Fiyeda hakan na samu kaina a lokacinda na samu labarin mutuwar yar uwata,rabin jikina,rayuwata,uwar Falaq Aziz wadda ayau zuciyarta take bugawa a kirjin 'yarku da kukaso ta rayu kuka kashe tawa rayuwar........ A cikin tsananin azabar datafi karfin kirjinsa Daddy mahmoud y dago idanuwansa da sukai jajir din azaba ya kalli AZIZ cikin tsananin mamaki da shock idanuwansa n fitowa sosai sbd azaba sa shock yana kallan fuskan AZIZ wanda sai a lokacin yake ganin kammaninsa da Yarinya me cikin da suka samarwa Jannah sbd akwai hotonta a cikin file din jannah har yau..... Magana yakeson yayi amma ina maganganun AZIZ ragargaza zuciyarsa sukeyi zuciyarsa na qara samun bugawa. Shi kansa AZIZ din cikin wani matsanancin halin yake magana yana fada masa yanda ya shiga cikinsu da yanda zai qarar dasu daya bayan daya ya tabbatarda ko sunansu aka fada sai an la'ance su an tsinewa zuriarsu. Kofa Sayd ya kalla sbd jin shigowan mota gidan ya tabbatarda Anny ce wadda ta iso gidan a gigice. Ko gani batayi sosai ta iso gidan sbd sakon daya shigo wayarta na cewa AZIZ LIMBA na hanyar isa Zaadens Daddy mahmoud ya nemesa zai basa takardun ciwon jannah daya buqata kuma tafi kowa sanin Sun goge sunan Ammar a cikin likitocin ciki daga nata saina sauran likitocin. A yanda tasan Familyn tsaf zasu cire sunan Ammar abar nasu hakama akan neman lafiyan jannah zasu iya fidda file dinta a bawa AZIZ LIMBA wanda hakan na faruwa sun gama Rayuwa a doran qasa sbd bazai rufa musu asiriba, Hakama matakin da Ammar yake kai yanzu na rashin lafiya harda kusan wadda ta shafi kwakwalwa take familyn zaa rifesa a matsayin baida lafiyar kwakwalwa ya sha ita kuwa fa?? Inaaa,bazata yadda ba wlh ko kadan.... Kwata kwata fita tayi hayyacinta taji bata gane komai bayan ta riga isa gidan kafin isar LIMBA. Gabaki daya ta fice hayyacinta sbd maganar Ammar datake yawo a cikin kanta wanda sai yanxu take kokarin tina kammannin donor din jan wadda take son hadawa da kammanin AZIZ din tanajin kanta na neman kuncewa. Kafafunta har rawa sukeyi ta iso palon daidai lokacinda Su AZIZ sun riga sun bar palon Daddy mahmoud ya daga hannu ya bude baki zai ambaci AZIZ din cikin tsananin azaba Anny bata tsaya lura da yanayinsa ba kawai ta dauka AZIZ din zai kira dan masa magana dan haka ta fidda allurar data taho da ita ta soka masa a wuya tana juye masa ruwan ciki daidai lokacin Saleem da mommy na shigowa palon shikuma AZIZ da sallama me nutsuwa ya qarasa cikin palon jannah wadda ke zaune shiru idanuwanta sunyi jajir ta qara fadawa sosai a kwana da wunin. Dago idanuwanta tayi ta kalli kofar jin muryansa da qamshinsa a lokaci daya. Ajiye kafafunta qasa tayi ahankali qasa tana kallansa a sanyaye sbd rabonta da ganinsa ko jinsa tin shekaran jiyan daya bar nan din. Takowa yayi ahankali cikin nutsuwa shima yana kokarin daidaita kansa daga halinda yake ciki na tafarfasan zuciya da tsananin ciwon zantukan daya maimaitawa zuciyarsa na yanda suka rabasa da Ummitah. Kallon dayake mata ne ya sakata miqewa ahankali tana jin zuciyarta na narkewa akansa taku daya tayi ta kasa ta tsaya tana kokarin faduwa qasa zaune ya tarota jikinsa yana kallan tsakiyar idanuwanta da suka kasa daukan kallansa ta lumshe su tana sauke ajiyan zuciya jiki a mace. Shiru yayi baice mata komai fuskanta kawai yake kalla yana jin yanda zuciyarta ke bugawa Kirjinsa.... Komai nata yana nuna yanda take tsananin sonsa ne wanda hakan yake masa illa mai girma a nasa bangaren sbd yasan soyayya zata iya zama rauninsa kaman yanda take rauninta... Ihun Mummy me karfin gaske ne ya sakashi lumshe idanuwansa ahankali ya budesa akanta ita kuma a lokacin ne ta bude nata idanuwan ahankali tana kallan kofa. Jame jikinta tai ahankali tana son zuwa palon amma batada karfin hakan a jikinta ko kadan dan haka ta kasa dagowa ta kallesa. Lura da hakan ya saka hannunsa ya zagoyo qugunta ta mannu da jikinsa ahankali ya dauketa gabaki dayanta a jikinsa ya nufo kofar da ita zuwa babban sitting room na gidan da hayaniyar ke fitowa ta can. Sayd shima a lokacin ya shigo palon kaman yanzu yake shigowa shima, Anny da hannuwanta ke rawa kallan Daddy mahmoud din dayake wani irin numfashi yana kokarin rasa ransa sbd Alluran datai masa kwata kwata baa yiwa wanda yake cikin heart attack hakan na matiqar hadarin gaske, Ganin su Mummy da Saleem akanta ya sakata fara rawar jiki tana kokarin daidaita kanta ta kalli Mummy tana cewa "Mummy koda nazo inaga ya samu attack ne ina kokarin basa taimako ne zamu iya gaggawan kaisa asibitin" Mummy bata iya amsata ba da gudun tayo kansa itada saleem tana ganin yanda yake wani irin jan numfashin wahala idanuwansa na rufewa shine ta fasa ihun me karfi tana kiran sunansa. A lokacin ne AZIZ da jannah din suka fito idanuwan Daddyn akan AZIZ yana kallansa wasu hawayen azaba da dana sani dana son ya fada musu waye AZIZ limba suka gangaro masa idanuwansa suka rufe ahankali cikeda azaba. Saleem ne da Sayd suka daukesa da gaggawa zuwa mota hakama jannah rawa jikinta yafara tana kallansu cikin tashin hankali da fargaban sabuwar masifar data tinkaro su. Fitowa sukai dukkaninsu harabar gidan yacewa Sayd yaje tareda Saleem ya taimaka masa shikuma ya karbi key din motarsa ya saka jannah a ciki motar saleem na fita tasa tabar mansion din shima ya nufi gida da ita. Mummy da duk ta fita hayyacinta take sbd tsananin tashin hankali daqyar Anny ta iya sakata mota itama a rude hannuwanta na rawa suka bi bayansu saleem din sai a lokacin take jin tsoron rashin tinanin datai na bin sakon da kyau taga inda ya fito ta jefa kanta cikin kaddara, Hakama waye wannan dayasan sirrin su bayansu dazai mata text din wanda takeda tabbacin yayi magana ne sbd yasan sirrin dasuke boyewa. Tin a mota saleem cikin damuwa da tashin hankali ya sanarwa Maheer suna hanyar asibitin da Daddy mahmoud. Miqewa Maheer yayi cikin tashin hankali yana kallan Dad daya ji abinda aka fada dukkaninsu hankalinsu na tashi da sabon tsoro. Koda aka iso asibitin da Daddy mahmoud gabaki dayansu Dad harda Mimi sun fito tareda tarin likitocin da zasu karbesa da nurses a shirye sbd gaggawar basa taimako sbd sanin shi din yanada matsalar samun attack. Dad da maheer idanuwansu sunyi jajir dad wani irin tsalle zuciyarsa keyi kansa na tsananin sarawa hakama maheer mimi kuwa duk ta rikice damuwa na qarar mata. Motarsu n shigowa asibitin da gudun gaske saleem ya iso emergency din da ita da gudu aka rufu kansu ana fiddosa hadda Sayd wanda fuskansa ke rufe sa facemask sbd Abraham da Ken na gurin. Yanda aka daukosa akai ciki dashi ne ya saka zaadens din gabaki dayansu shiga matsananciyar damuwar datafi ta farko sbd koda aka iso asibitin Rai ya riga yayi halinsa sedai hakuri. #MAMUH ZAFAFA BIYAR KALBIM 500 mamuhgee A DUNIYATA 500 Huguma AJIYA A DUHU 500 Billyn Abdul KIRJIN ME HANKALI 500 Miss xoxo Pay at 0022419171 AccessBank Maryam sani gummi Shedan biya 09033181070 Or mtn vtu at 09032345899*_KALBIM_* _Mamuhgee_ 78 *UMMU_MAHNOOR LUXURIES* (Best luxuries shop) 08034469681 08135142610 Aslm Alaikm ina kuke masu neman luxuries na kayan alfarmar kece raini? Ina masu son su saka sitirar alfarma ta zamani ta manyan mata masu aji da zaa kalleki kallo daya asan sitirar alfarma e kika saka? Shin kunsan me ake nufi sa kayan asalin yan gayu da nuna gayu? Sitirar Alfarma kikeson sakawa? Sitirar da kike ganin manyan mata da ita? Sitirarda zakiyi gayun sallah dake da yaranki a dauka waje kikaje da kanki kika siyota? To kizo ga damarki ta sameki sbd UMMU_MAHNOOR LUXURIES ta kawo miki sauki har gida, Karkice se masu kudi ke iya siya har kema me yar dama zaki samu naki da saukin kudi kuma best quality da kalar zamani data yan gayu, Nidai Mamuh nace duk wadda ke son a buga gayun sallan bana da ita da 'yayanta to tazo gurin UMMU_MAHNOOR LUXURIES tai siyayyar sallanta harma zuwa gaba dan nasan zakuji dadi da fahimtar abinda nake fada akan kayanta💯💯 Abubuwan da zaki samu a gurinta with the best quality na wayayyun mata masu aji yan gayu sune; Atampopi Laces Shadda Materials Shoes Bags Veils Trolleys Jewellerys Oil perfumes Numbers 08034469681 08135142610 Handles Instagram @ummu_mahnoor_luxuries TikTok username @ummu_mahnoor_luxuries Facebook ummu_mahnoor_luxuries ************* Mummy ganin yanda aka shige dashi itama taji kafafunta sun sare ta durqushe gurin tana fasa wani irin kuka mai tsananin gaske. Itama Mimi kasa tsayuwar tayi tai baya Saleem da hannuwansa ke rawa ne ya tareta jikinsa yana rungumeta sosai jikinsa tana fasa kukan datake cikinsa duk tsawon lokacin nan da rayuwar Ammar take neman lalacewa. Dzad ma Maheer ne ya riqesa da sauri a lokacin da Dr Abraham ya fito da sauri yana kallansu idanuwansa jajir sbd shima daddy mahmoud familynsa ne tinda ya dade da zama family ga zaadens, Cikin tsananin ciwon abinda zai fada kansa qasa yace "Sir Mzad ya riga ya tafi sai hakuri" Wani Rikitaccen kuka me tsuma zuciya mummy ta sake hakama Anny datake jin zata zare cikeda tsoro da tashin hankali. Mimi sake qanqame Saleem da hawaye ke gangaro masa itama tai. Maheer ma rawa jikinsa yakeyi gabadaya idanuwansa sukai jajir suna masa wani irin radadi me ciwon gaske hawaye na cika cikinsu amma basu saukoba. Dzad halinda daya shiga ya saka akai gaggawar yi kansa dan basa taimako kar ayi biyu sbd ba qaramar kauna me karfin gaske ce ba a tsakaninsa da dan uwansa da suka taso tare cikin gwagwarmaya ba uwa ba uba sai junansu da qanqarsu data fara tafiya tabarsu yanzu shima ya tafi ya barsa a lokacinda yake tsananin buqatansa sbd masifun da zuriarsu ke shiga batareda da sunsan ta inda abubuwan ke bullowaba. Asibitin kuwa kusan tsit tayi sbd masu ita sunyi mummunan rashin daya girgiza ahalin gabaki dayansu, Mummy kuwa Maheer ne ya dawo dashi da Mimi akanta suna kokarin ganin bata zare ba sbd yanda take kuka sosai kaman ranta zai fita. Koda akai awa daya da rasuwar tini labarin ya fara gauraya koina anata sanarwa a kafafen yada labarai cikeda jimami da Alhini ga zadeens da akasan yanda suke tsananin kaunar junansu fiyeda sauran families. A hanyar isowa gida Sayd ya kira AZIZ ya sanar da LIMBA Mahmoud Zad ya rasu. Shiru sukai dukkaninsu batareda kowa yace komaiba sbd basu dauka Allurar anny zata kashesa ba a yanda tsarin yake idan taxo alluranta qarasa paralysing nasa zatai bazai iya magana ba tsawon lokaci to amma basusan wace alluran bace tai masa data kashesa duk da sunsan ba imani ne da Anny dinba amma bai taba dauka zata iya kashe wani daga familyn nasu ba. Ahanya bude baki yace "Allah ya masa rahama" "Amin" Sayd ya furta yana qarasowa gidan. Koda ya iso gida yayi parking ya fito a bakin Latif yaji labarin rasuwar ya kallesa da mamaki sai a lokacin ya fahimci labarin rasuwar ya yadu kenan. Ciki ya iso ya wuce su mama a palo ya nufi palon AZIZ din yana isa ya sanar masa labarin rasuwar harya fita Jannah zata iya gani...... Sai a lokacin ya dago da idanuwansa ya kalli Sayd din. Ajiye wayar hannunsa yayi tareda miqewa ya fice daga palon kai tsaye ya nufi bedroom din jannah wadda ya ajiye yabaro tana kukan batason nan gidansu takeso. Yana isa dakin kai tsaye ya bude dakin ya shiga daidai lokacinda ta miqe tsaye da waya a hannunta kafafuwanta na daukan rawa kafin ganinta ya dauke ta saki wayar... Taku daya yayi ya dakatar da ita daga faduwan da zatai yana kamo fuskanta da hannunsa daya dayan kuma yana zagaye da ita a karan farko daya bude bakinsa ya ambaci sunanta a natse yana dan girgiza fuskanta. Bude idanuwanta da sukai jajir tayi tana kallansa ta fashe da wani irin kuka mai tsananin ciwo tana fixge jikinta daga nasa har tana baya da qarfi zata fadi ya sake dawo da ita jikinsa yana rasa abin fada mata sbd kukane takeyi sosai me sauti. Falaq ce da suka samu labarin itama ta nufo dakin da sauri ta taddata tana wani irin kuka me tsananin tsuma zuciya. Rasa ya zaiyi mta yayi gashi bakinsa baida abin fada dan haka ya matseta jikinsa a hankali yana jin yanda take turesa da karfi tana dukansa amma bai saketaba har saida ta gaji ta qamqamesa tana sake fasa sabon kukan dayake jinsa har cikin kansa. Falaq ma qarasowa tai ta rungumeta ta baya tana hawayen tausayinta da kuma tausayin Daddy mahmoud din daya rasu dukda bata san radadi da zafin rashi ba sbd koda ta taso batasan mamanta ba daddynta dasu mama ta sani kuma haryanxu bata rasa ko dayansu ba amma duk da hakan tana kwatanta zafin da akeji sbd idan ta kwatanta rasa dayansu jin takeyi kaman bazata iya daukaba. Tsit gidan limbas din yayi sbd jimamin tausayin Jannah da kukanta ke tashi a gidan cikin tsananin ciwon rashin datai sbd itama batasan radadin zafin rashi ba sai akan Daddy mahmoud din, Zuciyarta a cikin wani irin radadi da ciwo tareda qunci take daman shiyasa kukanta ya kasa daukewa. Ganin ta gaji da tsayuwar duk da a jikinsa take saiya zauna da ita tana jikin nasa tana cigaba da kukan falaq na gefenta tana shafa bayanta cikin tsananin tausayi da kauna me tsafta datake mata. Shiru sukai aka bata damar kukan har tayi ta gaji karfinta ya qare ya ciro wayarsa ya saka kiran Dr Sameera wadda tazo ta bata magani tai mata allura jikinta ya sake a cikin nasa alamar bacci ya dauketa. Sai alokacin ya dago fuskanta ya xuba mata idanuwansa yana kwatanta radadin da zuciya ke shiga a lokacinda ta rasa makusanci da kake kauna... Yasan tana cikin radadin rashinsa tinda ubane a gurinta wanda suka taso a cikin zunubi da haqqin rayukan da suke kansu sbd kaunarsu gareta amma ya tabbatarda radadin dasukeji qalilan ne akan wanda yake ciki har yau akan rashin rabin jikinsa da sune suka rabasa da ita, Baiso zuciyarsa ta kasance me tausayawa Ko mutum daya daga cikin ahalin nasu ba sbd halin da suka sakasa tareda ciwon dayake tattare dashi wanda har abada bayajin zai warke sai lokacin da Allah ya kaddari zaibi Yar uwarsa da iyayensa, Kuka sukeyi da jin azababben radadin rasa mutum daya da sukai a cikin su da sukeda yawa, Shi kuwa Ita kadaice dashi a duniyarsa kaf baida kowa bayan ita amma suka rabasa da ita.. Zareta daga jikinsa yayi ya kwantar yabar falaq ta rufeta ya fice daga dakin sbd a duk lokacinda wani zaiyi kukan rashi nasa radadin rashin dayayi ne yake dawo masa sabo tin daga kan mahaifinsa da Mahaifiyarsa zuwa kan Ummitansa da rashinta yake jijjiga rayuwarsa haryanxu. Su mama ma sanyi jikinsu yayi wanda ya saka kowa ma gidan jikinsa sanyi. Bacci tayi sosai na nutsuwar gangar jiki amma bana zuciya ba dan haka karfe uku tana farkawa Babu kowa a dakin ta kasa tashi tana neman wanda zai taimaka mata saiga Fiddausi tazo dubata sbd falaq na toilet. Itace ta qaraso da sauri ta kamata ta rakata har toilet ta fito tabarta. Ruwan zafi sosai ta gasa jikinta dashi wanda ya saka ta samu kuzari tai alwala ta fito ta shirya cikin doguwar Turkish Abaya tai sallah tana idarwa yana shigowa a shirye zai tafi janazah din da zaayi karfe hudu. Kallo daya tayi masa ta dauke kanta wanda ya sanasa fasa fadar abinda zai fada ya juyawansa ya fice. Yana ficewa ta miqe ahankali ta nufo kofa bayan ta zari key din motarta. Ko data iso palo ashe bai riga ya fice ba dan haka bata tsaya kallansa ba ta nufi kofa kokarin ficewa ya bude baki a natse yace "Ba inda zaki bakida lafiya so ki koma dakinki" Taso wucewa ta kasa tankasa sai kuma ta tina da idan taje gate ko zata mutu idan bai bada umarniba bazasu bari ta fita ba dan haka ta juyo ta kallesa idanuwanta na cikowa da hawaye ta maida idanuwanta kan mama sbd bama zata iya masa magana ba ta bude baki muryanta na rawa tace, "Mama inason na tafi gidan dan Allah" Mama da duk tausayinta yake sake rufeta kama hannunta tayi tana karban key din hannunta da kulawa tace "Maganar danake masa kenan yabarki kije,dan haka bakida lafiya bazakiyi driving da kanki ba can zamu dukanmu saimu tafi tare" Shiru tai sbd so tayi ta tafiyarta ga familynta ita kadai sbd suna tsananin buqatan juna a yanzu. Baice komaiba sbd umarnin mama koyaushe shine abinda baya musawa dan haka wucewa yayi gaba. Mama tura jannah din tai gurinsa suka tafi a motarsa ita kuma ta tafi a mota daban itada Baba alhassan, Falaq Daddynta yace babu inda zata daman itama tsoron zuwan takeyi hankalinta dik ya tashi. A mota babu me magana shiru har suka isa Zaadens a lokacin ake kokarin fara janazah din dan haka jannah ce kadai ta wuce cikin gida shikuma anan suka tsaya wajen ayi dasu. Tana shiga kai tsaye bangarensu Mummy ta nufa sbd kowa na can. Kallo daya taiwa Mummy da Mimi wasu sabbin hawaye suka zubo mata da gudu ta qarasa ta rungume Mummy wanda har karfinta tas ya qare gurin kuka. Anyi janazah din Mahmoud Zad a cikin radadi na rashinsa da akai an dawo, Bazasuyi zaman gaisuwa ba dan haka ana dawowa kowa ya watse sedai masu zuwa suna tafiya, Securities ne sosai acike da layin sbd manyan mutanen dake zuwa suna tafiya, Acan cikin gida ma babu mutane tsit ne duk wanda yazo yai gaisuwansa tafiya yakeyi sbd basason zaman da hayaniya kadaici sukeso. Su mama anan suka bar jannah wadda dataga da gaske zai iya cewa ta koma din kuma saita koma din dole ta roki mama ta sakasa barinta gidan ta kwana biyu. Dan haka acan aka barota daman shi tin daga gurin janazah bai dawoba ya wucewansa. Familyn Mummy dake Germany sun iso gaisuwa da tsayawa Mummy din wadda gaba daya ta shiga wani hali na rashin Mijin datake tsananin so yana tsananin sonta sbd itace bata haihuwa amma bai taba damuwa ko raayin aureba sbd samun haihuwa sbd kawai girman son da sukewa juna ya yadda ya zauna ba haihuwa yayan dan uwansa da yar uwansa sun ishesa. #MAMUH ZAFAFA BIYAR KALBIM 500 mamuhgee A DUNIYATA 500 Huguma AJIYA A DUHU 500 Billyn Abdul KIRJIN ME HANKALI 500 Miss xoxo Pay at 0022419171 AccessBank Maryam sani gummi Shedan biya 09033181070 Or mtn vtu at 09032345899*_KALBIM_* _Mamuhgee_ 79 *UMMU_MAHNOOR LUXURIES* (Best luxuries shop) 08034469681 08135142610 Aslm Alaikm ina kuke masu neman luxuries na kayan alfarmar kece raini? Ina masu son su saka sitirar alfarma ta zamani ta manyan mata masu aji da zaa kalleki kallo daya asan sitirar alfarma  e kika saka?   Shin kunsan me ake nufi sa kayan asalin yan gayu da nuna gayu? Sitirar Alfarma kikeson sakawa? Sitirar da kike ganin manyan mata da ita? Sitirarda zakiyi gayun sallah dake da yaranki a dauka waje kikaje da kanki kika siyota? To kizo ga damarki ta sameki sbd UMMU_MAHNOOR LUXURIES ta kawo miki sauki har gida, Karkice se masu kudi ke iya siya har kema me yar dama zaki samu naki da saukin kudi kuma best quality da kalar zamani data yan gayu, Nidai Mamuh nace duk wadda ke son a buga gayun sallan bana da ita da 'yayanta to tazo gurin UMMU_MAHNOOR LUXURIES tai siyayyar sallanta harma zuwa gaba dan nasan zakuji dadi da fahimtar abinda nake fada akan kayanta💯💯 Abubuwan da zaki samu a gurinta with the best quality na wayayyun mata masu aji yan gayu sune; Atampopi Laces Shadda Materials Shoes Bags Veils Trolleys Jewellerys Oil perfumes Numbers 08034469681 08135142610 Handles Instagram @ummu_mahnoor_luxuries TikTok username @ummu_mahnoor_luxuries Facebook ummu_mahnoor_luxuries ********* Ranar da akai kwana uku da rasuwar sawun ya zuwa gaisuwa ya dauke suka koma iya su familyn, Dad jikin nasa sai ahankali shima sbd damuwa me girman gaske ce ta cike zuciyarsa ya kasa cirewa dan haka gabaki daya walwalar familyn ta dauke basa cikin farin ciki ko kadan, Ammar ma andawo dashi gida sbd gabaki daya dai kansa ya juye suke gani haryanxu sunan AZIZ LIMBA ne a bakinsa. Mummy a ranar da akai ukun da yamma bayan angama addua ta buga waya cikin rashin bata lokaci saiga motocin Dss kusan guda biyar sun iso Zaadens sun zagaye gate din da gefen gidan. Anny suka taho kamawa a bisa tabbacin itace ta kashe Mahmoud Zad. Mummunan tashi hankalin Su Dad da maheer yai harma da Mimi da dukkaninsu. Sai a lokacin Mummy ta fito ta nuna babu wani sulhu ko tsayawa sauraron bayani komai Anny ce ta kashe Mahmoud kuma dole zata karbi hukuncin hakan sbd a gaban saleem ne shima gani, Jannah ma da mijinta sun gani hakama yan aiki duka shaida ne, Zata tabbatarda Anny ta karbi hukuncin kisa akan abinda tai idan kuma akwai wanda ya isa ya tsaya mata zasusha mamakinta sbd gabaki daya dukiyarta da itace share dinsu datake riqe dasu ayanxu zata janye ta kuma yi sharia dasu da dalili a lokacinda basuda karfin ko power din iya fada da ita sbd sunsan ita din ko wace. Wannan itace sabuwar masifar data diro musu wadda ta saka yan jarida fara yada labarai akan zaadens din. A lokacin da zaa tafi da Anny din kasa yadda tayi da hakan tai gaggawar boyewa bayan bayan Maheer tana riqesa hannuwanta na zuba wata irin rawa cikin matsanancin tsoro da tashin hankali me girma tace "Maheer wlh banyiba,dan Allah karka bari su tafi dani, Bazan iya zuwa prison ba dan Allah karka bari su tafi dani" Komawa tayi kan Mimi tafara rokonta idanuwanta kaman zasu fito sbd tashin hankali da firgicewa. Kan dad ta koma ta zube qasa tana kama kafafunsa cikin tsananin kukan tashin hankali tana cewa "Dad wlh bansan zai rasa ransa ba,banyiba dan Allah karka bari su tafi dani" Mummy da idanuwanta suka gama rufewa da tsananin fushi da bacin rai me tsananin gaske takowa tayi ta dago Anny din ta saukar mata da lafiyayyan marin daya sakata zubewa qasa hancinta na zubo da jini. Da sauri Maheer yayi kanta ya dagota jikinsa yana rungumeta ya dago ya kalli Mummy din idanuwansa jajir yace "Mummy baa zartar da hukunci a cikin fushi batareda bincike me kyau ba, Tayaya zamu bari muna matsayin family irin wannan matsalar me girma ta fita zaa iya bincike a gane a magance cikin gida......." Cikin mamaki sa sabon bacin rai Mummy ta kallesa kafin ta maida kallanta kan Dad daya kasa cewa komaiba sbd yafara jin inama shine yabar duniyar ya huta da wannan baqin cikin dayake zuwa wani bayan wani Tace "Dzad kanajin abinda Maheer yake fada akan mutuwar dan uwanka wanda kake ikirarin rabin jikinka bakada kamarsa? Kana jin yana cewa a rufe maganar wadda ta kashe Mahmoud sbd tana matarsa, Wannan shine adalci ko sakamakon da Mahmoud zai samu daga gareku?bayan duk sadaukarwa da zunuban daya dauka sbd kai da yayanka Dzad? Wasu hawayen baqin ciki ne suka zubo mata a cikin tsananin fushi ta fixgo Anny ta jefawa Dss da take suka kameta aka saka mata cuffs tana wani irin kuka da ihun tashin hankali me tsananin gaske sbd tsoron a kasheta itama. Dad dagowa yayi ya kalli Mummy ya bude baki yace "Nafeesat nasan Zuciyarki tana cikin zafi da radadin rashin Mahmoud kaman yanda nake ciki amma hakan bashine mafita ba, Qarawa kanmu matsaloli zamuyi bayan bamu magance na gabanmu ba, Zamu bari duniya tai mana dariya ne maqiyanmu zasu samu damar sake cutatar damu dan haka ki janye ya saki Anny zamu ji da matsalar a nan cikin gida" Kallan dayake kama dana tsana Mummy kewa Dzad din tana jin baqin cikin sadaukarwa da zunuban da Mahmoud ya ringa dauka akan dan uwansa harya bar duniya gashi yanxu dan uwan nasa ne ke bude baki yana cewa ayi shiru akan wadda ta kashesa. Bata iya cewa komaiba juyawa tai tabar gurin ta nufi bangarenta bayan anwuce da Anny wadda ta zare take. Mimi da idanuwanta suka bushe har hawaye sun qafe mata juyawa tayi ta koma ciki jikinta a tsananin mace kirjinta na mata ciwo itama. Jannah ma bayan Mimin tabi itama kirjinta na matsa tsananin ciwo me dacin datake jinsa har bakinta. Maheer kadai aka bari harabar gidan bai iya motsawaba yana jin duniyar na juyawa dashi sbd tsananin quncin daya rufe zuciya da idanuwansa gabaki daya. Mummy Former spokesperson a Germany hakama ta zauna matsayi me girma a italy dan hakama familynta duka yan boko ne sosai dasukeda manyan matsayi da arziki sosai itama dan haka koda ta dena aiki tana da arziki sosai wadda ta zuba rabinsa a business din zaadens dan haka kusan arzikin zaadens din tanada share me girma a cikinsa, Yanzu daga baya da suka samu matsalar da aka samu sauran shares dinta dake wasu manyan companies ne ta karba ta bayar aka hada maja da LIMBAs dan haka a wani bangaren dai kusan dukiyarta ce yanzu a zaadens din take riqe dasu hakama tanada sauran kadarori da wasu shares din masu girma a wasu guraren dan haka kai tsaye a yanzu a halinda suke ciki sunsan ja da ita zai musi wuya shiyasa dole lallabata zaayi ta janye dan basuda power din fada da ita da familynta. Kwanan damuwa me tsanani akai a zaadens wanda ya saka jannah tashi da rashin lafiya. A waya falaq taji yanayin Jannah dan haka ta shiga damuwa itama. Karfe goma da mintina Su Dr Abraham sika iso Zaadens sbd yanayin jannah wadda haryanxu ma basu samu dubata dinba. A daki na musamman da aka ware sbd jinyar family members na zaadens tamkar a asibitin lafiyayye acan aka kai jannah wadda ta laushi sosai sbd damuwar datai mata yawa. A daidai wannan lokacin ne motar AZIZ LIMBA ta iso gidan aka bude masa gate ana masa barka da zuwa. Parking Sayd yayi ya bude masa ya fito suka nufi ciki Saleem daya fito tarbansa ya gaidasa cikeda girmamawa suka nufi dakin da aka kai jannah din. Abraham ne yake dubata dan haka hankalinsa gabaki daya yana kan Jannah din... Ken dayake tsaye yana duba monitoring heart dinta a injin kaman a mafarki idanuwansa suka dago cikin slow suka fara sauka akan fuskar AZIZ AY LIMBA wanda ko zaa zare ransa a dawo masa dashi bazai mantasa ba, Kasa motsawa yayi kansa da jinin dayake yawo a jikinsa suna tsayawa daga kowane motsi ahankali idanuwansa akansa kaman yanda yake kallansa shima idanuwansa a cikin nasa suke yana masa kallan dayake dauke masa ji da ganin komai daidai. Bayyanar Sayd a bayan AZIZ din ya saka hannuwansa sakewa Sai ganin akai jini na gangarowa daga hancinsa ahankali me kauri. Cikin Mamaki da dan fargaba Dzad ya ambaci sunansa yana kallan hancinsa. Sayd ne ya tako kafin Ken din ya motsa daga mummunan shock din daya saka hancinsa barewa da jini, Handkerchief ya fidda daga aljihunsa fari qal bai tsaya komaiba a natse ya ya dora masa a hancinsa yana rufewa cikin sautin da babu wanda yajisa yace "Akwai Enzoskillienia datake cikin Handkerchief dinnan wadda bazata bari jinin hancinka ya tsayaba har jininka ya qare katafi inda baa dawowa, If you want the antidote act just act normal" Janyewa yayi Ahankali daga gabansa yana cewa "Sorry doc" Wani irin rikitaccen Juyawar cikin data sanya amai taso masa ne ya sakasa barin dakin kafafuwansa na wata irin rawa hancinsa na sake zubo da jini sosai ganinsa yana rikicewa sbd tsananin tashin hankali da shock. #MAMUH ZAFAFA BIYAR KALBIM 500 mamuhgee A DUNIYATA 500 Huguma AJIYA A DUHU 500 Billyn Abdul KIRJIN ME HANKALI 500 Miss xoxo Pay at 0022419171 AccessBank Maryam sani gummi Shedan biya 09033181070 Or mtn vtu at 09032345899*_KALBIM_* _Mamuhgee_ 80 *UMMU_MAHNOOR LUXURIES* (Best luxuries shop) 08034469681 08135142610 Aslm Alaikm ina kuke masu neman luxuries na kayan alfarmar kece raini? Ina masu son su saka sitirar alfarma ta zamani ta manyan mata masu aji da zaa kalleki kallo daya asan sitirar alfarma  e kika saka?   Shin kunsan me ake nufi sa kayan asalin yan gayu da nuna gayu? Sitirar Alfarma kikeson sakawa? Sitirar da kike ganin manyan mata da ita? Sitirarda zakiyi gayun sallah dake da yaranki a dauka waje kikaje da kanki kika siyota? To kizo ga damarki ta sameki sbd UMMU_MAHNOOR LUXURIES ta kawo miki sauki har gida, Karkice se masu kudi ke iya siya har kema me yar dama zaki samu naki da saukin kudi kuma best quality da kalar zamani data yan gayu, Nidai Mamuh nace duk wadda ke son a buga gayun sallan bana da ita da 'yayanta to tazo gurin UMMU_MAHNOOR LUXURIES tai siyayyar sallanta harma zuwa gaba dan nasan zakuji dadi da fahimtar abinda nake fada akan kayanta💯💯 Abubuwan da zaki samu a gurinta with the best quality na wayayyun mata masu aji yan gayu sune; Atampopi Laces Shadda Materials Shoes Bags Veils Trolleys Jewellerys Oil perfumes Numbers 08034469681 08135142610 Handles Instagram @ummu_mahnoor_luxuries TikTok username @ummu_mahnoor_luxuries Facebook ummu_mahnoor_luxuries ********** Dr Abraham ne ya dago ya kallesu shima sedai bai gane Sayd ba sam dan haka hankalinsa kwance ya gaisa da AZIZ din kafin ya fice daga dakin dauke da file din Jannah wanda idanuwan AZIZ din sukaiwa kallo daya. Gaisawa yayi da dad kafin ya kalli jannah din wadda take kwance a sanyaye. Ficewa dad yayi saleem da sayd sukabi bayansa aka barsu su kadai a dakin. Zuba mata idanuwansa yayi ita kuma taqi bude idanuwanta ta kallesa. Shiru sukai tsawon lokaci sai kawai jin tayi ya daka hannuwansa ya dauketa ahankali ya fice da ita. Koda ya fito ba kowa duk suna bangaren dad dan haka kai tsaye yayi mota da ita suka nufi gida. Dr ken da tashin hankali me tsananin gaske da shock suka hana jinin hancinsa tsayawa hankali tashe yabar zaadens jikinsa na tsananin rawa ko gani sosai bayayi yabi motarsu AZIZ din. Sayd yagansa a bayansu dan haka baice komaiba har saida suka isa limbas security suka hanasa shiga saida sayd din ya fito yace abarsa ya shigo amma banda motarsa. AZIZ ciki yayi da jannah yakaita har dakinta ya ajiye juya ya fice falaq na murnan dawowanta. Sayd ne ya iso palon baqi da ken wanda jikinsa ne tsananin rawa jikinsa duk ya baci da jini. Kallo daya yayiwa AZIZ yaji hankalinsa na sake tashi duk da bai yadda da sunsan abinda ya faruba akan rasuwar Ummitan. Ahankali sayd ya iso gabansa ya jiye masa file din farko dayake nuni da a rubuce aikin da akai na zuciya tsakanin UMMITAH ABDULAZIZ zuwa ga JANNAH ZAD a asibitin zadeens da sunayen likitocin da sukai tareda date din da time wanda a gurin matar dr ismail aka samu da stamp na asibitin zaadens a jiki a cikin file din jannah ya saci copy din kamar yasan ranar zatazo. Karatu daya dr Ken yayiwa takardan zaiyi magana Sayd ya daukesa da wani mahaukacin marin daya qarasa balle hancinsa da jini ya kifu a qasa hannuwasa na rawa. Takarda ta biyu sayd ya fidda ya sake ajiye masa a gabansa wadda take dauke da adadin kudaden da aka basu a lokacin aikin da date a jiki da komai. Rawa jikin dr ken ya sake dauka ya bude bakinsa dayake tsananin rawa yana son ambatar sunan AZIZ Latif dayake palon tsaye shima ya kifa masa wani azababben mari yana cewa "Kada ka sake bakinka ya furta sunansa sbd hakan na faruwa wlh baxaka futa da hakori ko daya a gidan nan ba" Sayd da koina jikinsa ke rawa dagasa yayi sama ya buga da qasa yana taka wuyansa da kafarsa yace "Me kakeson fada? Yanda kuka kasheta?? Yanda ka siyar da zuciyarta? Wani mummunan naushi Latif yayiwa zuciyar ken din sayd na rufe bakinsa yana hanasa ko fidda numfashin wahala. Miqewa AZIZ yayi yana barin palon sbd yanda zuciyarsa ke ingizashi ka fasa kirjin ken din ya rabasa da tasa zuciyar shima. Wani irin azababben dukan daya rabasa da hakoransa uku na gaba sukai masa saida yakai baya iya bude idonsa daya daya tsiyaye kafin latif ya miqar dashi... Kallansa sayd yayi yace "Wannan dukan nawa ne, Bazaka iya daukan na Limba ba dan haka ya baka damar wanke kanka ta hanyar kawo mana file din jannah kota halin yaya kafin karfe goman safen gobe, Idan ka kawo mana zaka bar qasar ka koma ga iyalinka kai ka fita a cikin case din" A jikinsa na rawar azaba da tsananin radadin zuci da jiki ya gyada kai bayan ya musu kallan sun tabbatar, Gyada masa kai Sayd yayi yana basa tabbacin hakan. Latif ne yakaisa har gidansa da knsa sbd ya gyara kansa kafin ya nufi gidan Abraham wanda file din yake hannunsa. AZIZ da sayd ya sanar masa bude baki yayi a natse yace "File na shiga hannunmu a goben a sakarwa yan media komai dayake cikinsa, Copy daya kuma a aika a Germany gurin dr Nico zai gabatarwa babbar qungiyar lafiya tareda sunayen duka patients da mutanen da aka cire zuciyoyinsu." Gyada kai sayd yayi yana saka Fahad hada kan manyan channels su shirya karban news din. **a daidai wannan lokacin kuma acan zaadens Maheer ya fita hayyacinsa sbd duk wata hanyar da zasu bi sunbi akan case din Anny amma sam ba haske case din me girman gaske ne da manya suke backing nasa ciki harda AZIZ LIMBA wanda ya hana a karbi duk wanda zaizo duba Anny din. Mummy ta bar zaadens sbd ta shirya fada dasu iya inda karfinta zai Kare saita tabbatarda Anny tabar duniya kaman yanda Mahmoud ya bari. Ammar ya qarasa rikicewa duk iya karfinsa yakeson fadawa su daddy waye AZIZ amma sam sun kasa barinsa magana allurai kawai ake masa sbd kada ya tona musu asiri gurin surutansa. Karfe goma sha Biyun dare Dr ken ya baro gidan Dr Abraham daya cewa accident ya samu ya gama dubasa da dressing masa koina ya shige toilet a lokacin ne Dr ken ya samu damar dauke file din y fice yabar gidan. Kasa tafiya yayi dashi gidansa sbd duk rintsi bazaiso asan shine ya dauka ba dan haka Sayd ya kira a cikin daren ya basa. Sayd na karba ya kasa budewa yayi sbd yanda jikinsa yayi tsananin sanyi zuciyarsa ma na yin sanyi da mutuwar jiki sbd wannan shine file din dayake dauke da hoton Ummitah na karshe a duniya acikin kayan tiyata. Yana isowa gida yayi parking ya kashe motar tareda juyowa ahankali ya kalli file din dayake cikin wata jaka cikeda sirrikan mutuwar mutane da dama, Wasu iyalansu suna cikin qunci haryanzu wasu kuma haryanxu iyalansu basusan suna raye ko mace ba, Ahankali ya miqa hannunsa ya dauka ya ciro file din tareda budewa hannuwansa na wata irin rawa sbd radadin mutuwar matarsa data dawo masa sabuwa wadda akanta ne haryanzu bai dawo daidai ba shima, Shafi shafi yafara wucewa yana kallan fuskokin mutanen da aka raba da rayukansu akan rai daya, Jajir idanuwansa ke qarawa yana jin kaman bazai iya kallan na Ummitah ba.... A shafin karshe yana budewa hoton Ummitah ya bayyana Wani irin kuka ne yazo masa me karfin daya sakasa rufe bakinsa da hannunsa daya yana ajiye file din da sauri sbd sanye take da kayan patient da shine ya saka mata su da hannunsa a lokacinda akace cs din cikin jikinta zaayi mata, Idanuwanta a rufe suke sedai hasken dayake kan fuskanta kana gani kasan na barin duniya ne, Kuka yakeyi sosai wanda rabonsa da yinsa tin ranar rasuwarta, Ya jima a motar yanayi kafin ya fito daqyar kafafunsa da sukai sanyi sosai suna dagawa cikin sanyi da mutuwar jiki ya isa palon AZIZ gidan tsit kowa ya shige. Ahankali batareda ya iya dagowa ya kallesaba ya ajiye masa file din gabansa ya juya ahankali ya fice yana kasa cewa komai. Shi kansa bayan ficewan Sayd zubawa file din idanuwansa yayi tsawon lokaci batareda ya motsa ba kafin yakai hannunsa ahankali ya dora akan file din zuciyarsa tai wani irin sauke numfashi mai sanyi yana danne abinda yake taso masa cikin maqoshinsa. Daukan file din yayi yafara bude shafin farko hoton yaro ne qarami da baifi shekaru ashirin ba wanda shine victim na farko da aka fara qunsawa familynsa baqin cikin da har abada bazai barsu ba.... Wani irin nauyi kirjinsa yayi yafara wucewa ahankali ahankali yana kallan fuskokin mutanen da an kashe basa duniya.... Hankalinsa tashi yayi sosai sbd bai dauka an kashe rayuka d yawa haka ba dan haka hannuwansa suka fara dayazo shafin karshe dakatawa yayi hannuwansa na tsananta rawa bugun zuciyarsa na wani irin tsananta da tsananin zafi da ciwo, Bude na karshen yayi wanda fuskar Ummitansa ta bayyana bugun zuciyarsa yayi wata irin tsayawa yana rintse idanuwansa da cikin tsananin ciwon daya soki kirjinsa ya kasa kalla ya saki file din Hannuwansa da wata irin rawar data sakasa miqewa zai isa bedroom dinsa neman Maganinsa da sauri kafin yayi loosing amma taku biyu yayi kafafunsa suka buge suka zubar dashi palon da karfin gasken daya saka Jannah data fito zuwa dakin Falaq ta kwana acan sbd damuwa take ciki sosai ta kwana dakinta. Dakatawa tai daga inda take tana wai waiwayowa ta kalli kofar palonsa. Wani irin yunquri yayi da karfi idanuwansa na sauyawa gaba daya ya miqe sedai sake faduwa yayi akan console dayake gurin da karfin daya fasa hannuwansa da gefen bayansa jini yafara fita... Tafiya ta fara zuwa inda zata har tayi taku biyu taji bazata iya ba, Cikin tsoro ta juya ta nufi palon gabanta na faduwa ta miqa hannunta ahankali ta bude kofar kai tsaye a karon farko kenan zuwanta ita kadai gurinsa. Akansa idanuwanta suka sauka tsoro ya kamat gabanta yayi mugun faduwa ta nufesa da sauri a lokacin dayake kokarin sake tashi jikinsa gabaki daya yana wani irin rawar data sakata tsoro da Fargaba ke girma sbd bata taba ganin ko Ammar a cikin irin wannan halinba idan ciwonsa ya tashi, Da sauri ta dora hannuwanta akansa daidai lokacin dayake sake miqewa ya nufi bedroom dinsa da sauri ta bude mas kofar Bedroom din tana riqe dashi suka nufi toilet data fahimci can yake tsananin Buqatan zuwa. Suna shiga kasa isa yayi daqyar ta isar dashi sbd zuwa lokacin yayi loosing gabaki daya. Hannunta na rawa ta kunna musu ruwan dumi suka fara sauka akansu yana mata wata irin qanqamewan datake jin kaman zata balle amma jin tai zuciyarta na mutuwa da tsananin sonsa da tausayinsa sbd yanayinsa dayake neman kasheta da tsoro da tausayi, Qanqamesa itama tayi tana kare fuskasa da tata fuskan sbd ruwa kada su shigar masa hanci dan haka hancinsu yana gogan juna ta sake qanqamesa tana karban azabar dayake bata da irin riqon da yayi mata batareda yana hayyacinsa, Neman juyewa kansa yayi yana sake qanqameta komai nasa na wata irin rawar dake saka hawaye biyo fuskanta tana sake hade fuskansa da nata tana jin kaman duk abinda yakeji ya dawo jikinta ya samu sassauci, Sun jima a hakan tsawon lokaci kafin ya samu sassauci komai yafara lafa masa ahankali. Shiru sukai a yanda suke yana rungume a jikinta tsawon mintina kafin ya bude idanuwansa ahankali jajir dasu ya saukar a fuskanta datake hade da tasa, Ahankali ya saka hannuwansa ya zagota jikinsa da kyau yana bata damar zama akansa har lokacin fuskansu yana hade... Ahankali tayi baya ahankali tana janye fuskanta daga tasa tana baya da kirjinta dayake hade da nasa ya dawo da ita ahankali yana kallan yanda ruwa ke sauka akan fuskanta ahankali suna gangarowa zuwa dogon hancinta da lips dinta da sukai wani haske. Bin ruwan yayi da kallo suna shiga har cikin bakinta suna saka lips dinta motsawa. Motsawa tai ahankali kirjinta yayiwa kirjinsa wata irin shafar data sakasa bin kirjin nata da wani kasalallen kallo sbd karfinsa bai gama dawowa ba. Rigar baccin dake jikinta lafewa tai a jikinta sbd ruwa gashi bata sanye da bra dan haka abinda idanuwansa ke kokarin sauka akaine ya sakata saurin saka tafin hannuwanta duka biyu masu sanyi da laushi ta tallafe fuskansansa dan sedai kafin tai wani motsi daga hakan ya fixgota daga zaunen da suke ya hade bakinsa da nata yana zira harshensa ciki tareda ruwan dake zubo musu. #MAMUH #THE STORY BEGINS #BEST LOVE AND REVENGE STORY #AZIZ LIMBA #AMMAR ZAD #JANNAH ZAD ZAFAFA BIYAR KALBIM 500 mamuhgee A DUNIYATA 500 Huguma AJIYA A DUHU 500 Billyn Abdul KIRJIN ME HANKALI 500 Miss xoxo Pay at 0022419171 AccessBank Maryam sani gummi Shedan biya 09033181070 Or mtn vtu at 09032345899*_KALBIM_* _Mamuhgee_ 81 *UMMU_MAHNOOR LUXURIES* (Best luxuries shop) 08034469681 08135142610 Aslm Alaikm ina kuke masu neman luxuries na kayan alfarmar kece raini? Ina masu son su saka sitirar alfarma ta zamani ta manyan mata masu aji da zaa kalleki kallo daya asan sitirar alfarma  e kika saka?   Shin kunsan me ake nufi sa kayan asalin yan gayu da nuna gayu? Sitirar Alfarma kikeson sakawa? Sitirar da kike ganin manyan mata da ita? Sitirarda zakiyi gayun sallah dake da yaranki a dauka waje kikaje da kanki kika siyota? To kizo ga damarki ta sameki sbd UMMU_MAHNOOR LUXURIES ta kawo miki sauki har gida, Karkice se masu kudi ke iya siya har kema me yar dama zaki samu naki da saukin kudi kuma best quality da kalar zamani data yan gayu, Nidai Mamuh nace duk wadda ke son a buga gayun sallan bana da ita da 'yayanta to tazo gurin UMMU_MAHNOOR LUXURIES tai siyayyar sallanta harma zuwa gaba dan nasan zakuji dadi da fahimtar abinda nake fada akan kayanta💯💯 Abubuwan da zaki samu a gurinta with the best quality na wayayyun mata masu aji yan gayu sune; Atampopi Laces Shadda Materials Shoes Bags Veils Trolleys Jewellerys Oil perfumes Numbers 08034469681 08135142610 Handles Instagram @ummu_mahnoor_luxuries TikTok username @ummu_mahnoor_luxuries Facebook ummu_mahnoor_luxuries ********** Kai tsaye ruwan dayake shiga bakinta yafara zuqa ahankali a cikin bakinsa ya hadiye ahankali suka bi ta maqoshinsa cikin wani irin sanyin daya saka maqoshinsa wani irin kukan wucewan abu me girma a maqoshin a hankali, Bude jajayen idanuwansa da sukai sake jijir yayi ya kalli idanuwanta data rintse da karfi, Wani slow idanuwansa sukai akan hancinta suna gangarowa zuwa lips dinta dake hade da nasa kafin ya ware bakinsa a hankali gabaki daya yana shiga bakinta da kyau yayiwa duk abinda yake cikin bakinta wata irin zuqan data sakata barin jikinsa ya sake zagayo qugunta da hannunsa yana mannota da karfi jikinsa kirjinta yayi wani irin sauka a kirjinsa ya sakar masa wani lafiyayyan shock din daya sakasa sake kutsawa cikin bakinta yana mata wani irin shan dayake juyar da qwaqwalwansu su duka, Cikin wuyanta ya gangaro da kansa yana bin fatar wuyanta da harshensa dayake da dumi yana shan ruwan dayake bin wuyanta ahankali yana gangarawa kirjinta da halittarsa take bayyane fes sbd rigar data gama mannewa a jikinta ta gama tona asirin halittar komai dake jikinta. Xubawa kirjinta jajayen idanuwansa yayi kafin ya dagosu ya kalli fuskanta wadda tai jajir idanuwanta a rufe har lokacin, Saukar hannunsa akan rigarta ya sakata bude idanuwanta da sukai jajir itama ta kallesa shima ita yake kalla dukkaninsu a wahalce, Zame rigar yayi ta bangare daya zuwa qasa tayi saurin dora hannunta akan nasa ahankali tana rufe idanuwa ahankali wani irin numfashi me sanyi na fito musu lokaci daya...nata na sauka a cikin kunnewansa nasa kuma ya sauka a fatar wuyanta data saka tsigar jikinta tashi ta bude idanuwa ahankali daidai yana zare rigarta ta sauka daga kafadunta har zuwa kirjinta. Rungumesa tayi da sauri cikin wani irin mutuwar jiki da tsananin kunya, Shi kuwa rigar jikinsa ya saka hannu ya barka ahankali wanda ya bawa asalin fatar kirjinsa da nata haduwa a cikin ruwan dumin dayake sauka har lokacin ahankali duk da ya miqa hannu ya kashe bai rufe daidai ba dan haka har lokacin ruwa na sauka ahankali kadan kadan. Saukar kirjinta a asalin lafiyayyan fatar jikinsa ya saka bayansa fadawa jikin bangon bayansu yana zagayo bayanta da tafin hannuwansa yana dago kansa ya sake kama bakinta ahankali yana zira harshensa cikin bakinta ya laso taste din bakinta kafin yafara kissing din bakin yana tsotsanta da wani irin yanayin dayake gangar jikinta rawa da tsoron jin irin riqon dayayi mata da wani irin karfin dayake saka gangar jikinta rawa da tsoron irin girman karfin datake ji a tattare dashi wanda ta tabbatarda hadda na ciwonsa kila amma kuma zuciyarta dake karban kowane sakon dayake isowa daga garesa tana jin zuciyarta bata karbi tsoro da fargaban da gangar jikinta ke shiga ba. Wata lafiyayyar runguman dayawa qugunta yana sake matseta da jikinsa saida wani qashinta ya amsa ta qanqamesa da karfi tana rintse ido tanajin yanawa harshenta wata tsotsan daya kusan juyar mata da kwakwalwa. Cikin wuyanta ya dawo da kansa yana jefa mata wani numfashi me dumin gaske tareda dumin harshensa dayake bin fatarta yana kashe toshe mata kwakwalwa dip, Saukan bakinsa a kirjinta ya saka numfashinta daukewa cak Daqyar ta iya bude idanuwanta a tsananin wahalce tana janye jikinta daya kasa janyuwa... A yanda suke ya miqe da ita a jikinsa yana fita hayyacinsa hannuwansa da dukkanin jikinsa na wata irin rawar dayake jin kaman zai kakkaryata a jikinsa, Lafiyayyan gadonsa dayake a tsare da tsadaddun beddings ya zaunar dasu tana kan qafafunsa ya sake hade bakinsu yana kissing dinta koina nasa na rawa sosai gabaki daya jijiyan jikinsa sun fito harna hannuwansa dana dantsen hannuwansa da suka sakata rufe idanuwanta ahankali sbd ta tabbatarda yana loosing control ne dan haka tai saurin rungumesa tana karban kissing din dayake mata...... Saukar tafin hannuwanta a fatar bayansa ya sakasa juyawa da ita yana lasar fatar bayanta ahankali hannuwansa na zagayo cikinta da kirjinta wanda ya sakata fidda wata qaramar qarar data sakasa birkitota yana sake hade bakinsu kafin ya juyata a jikinsa ya kwantar a lafiyayyan gadon yana bude idanuwansa da suka jikinta fara rawa a hankali sbd kwata kwata bataga AZIZ LIMBA data mutu akansa ba, Wani daban tagani wanda ya riga yayi loosing control akwai yiyuwar rasa gabobin jikinta da kanta gabaki daya rawa jikinta yakeyi ahankali koina nata na daukan dumin abubuwan dasuke faruwa a daidai wannan lokacin amma zuciyarta na jin kaman bazata gujesaba duk da tasan tana cikin hadari haduwa dashi a wannan yanayin nasa...... Yanda jijiyoyin jikinsa suka bayyanarda lafiyayyan karfinsa da yanda jikin yake rawa idanuwansa jajir ya saka wasu hawaye masu tsananin dumi gangaro mata tana lumshe idanuwanta tareda saka hannuwanta biyu ahankali ta zagayo wuyansa tana saka bakinta a cikin nasa da kanta sbd samar masa da sassauci da samun control ko yayane. Kissing dinsa takeyi tana sake zagayosa ahankali cikin sanyi da nutsuwa da tsananin sonsa daya gama illatata.. Control din yafara samu ya matseta jikinsa yana karban komai a natse har saida ya samu control dinsa ya dawo kafin ya karbi ragamar komai ta hanyar saka hannuwansa yana rufe kirjinta da tafin hannuwansa yana kissing din bakinta a hankali. Komai ya daidaita ahankali cikin wani irin yanayin dayake tsananta gudun hawayenta ya kwantar da ita da ya miqa hannunsa ya kashe kashe ac din dakin da remote sbd sanyin dayake ratsata yayi mata yawa. Harshensa ya zira a cikin kunnenta yai mata wata irin lasan data sakata qanqamesa tana manna masa kirjinta Batareda ta saniba, Bude idaniyarsa yayi ya kalli fuskansa yana nufar bakinta da nasa ahankali ya hade yana tsotsa cikeda shirin maidata cikakkiyar mace....sedai kafin yayi wani motsi aka buga kofar dakin da karfi tareda kiran sunansa. Wata irin mummunan sarawa kansa yayi wanda ya sakasa rintse idanuwansa da karfin gaske yana zubewa gefe hannunsa na dan rawa. Jannah kuwa mummunan faduwa gabanta yayi ta rintse idanuwanta hawayen dake cikinsu suka gangaro tana dawowa hayyacinta tsaf. Sake buga kofar Falaq tai tana ambatar sunan daddynta cikin damuwa sosai a bayyane tace "Daddy, Jan bata nan ta bata a cikin daren nan munata nemanta bata koina a cikin gidan nan fiddausi ta duba koina kafin ya tadani kuma mun duba koina mama tace a kiraka ga securities can uncle ya tara duka baa gantaba." Rintse idanuwansa ya sake yi yana jin duk abinda falaq din ta fada.. Jannah jin duka gidan an tashi ana nemanta ya sakata samun kanta a cikin matsanancin hali na kunya da danasanin zuwa dakin tin farko, Bai juyo ya kalleta ba ya sauka gadon tareda nufar closet dinsa ya zare dogon wandon dayake jikinsa da sanyin ruwan toilet har lokacin ya sauya kaya zuwa black balmains sweatset na bacci masu kauri. Riga da wandonsa da sukai mata tsananin yawa ya dauko ya bata ta tafi closet din nasa inda baa ganinta itama ta saka gashin kanta duk a jiqe ta daure da qaramin towel tana kasa nufar kofar da har lokacin falaq ke bugawa. Batareda ya kalleta ba ya bude baki a natse da muryansa da bata gama dawowa daidaiba yace "Kije ke ake nema" Juyowa tai ta kallesa da sauri zuciyarta na tsinkewa sbd bazata iya fitan ba bayan ance kowa ya tashi ita ake nema sai kawai a ganta ta fito dakinsa da kayansa a jikinta gashinta da ruwa, Me zata cewa mama da baba Alhassan? Da wane ido zata kalli falaq? Yaya su Sayd da securities zasuji daga inda ta fito? Fiddausi da aka fara cewa taje taga bata gantaba tayaya zata fara kallanta bayan duk dare kafin safe aka saka Fiddausi dubota so uku sbd ciwonta har saita warke, Yanzu kawai taxo bata gantaba har toilet kowa ya tashi sai ace ga inda ta fito. Ganin bata iya motsawa ba ya sakasa juyowa ya kalleta yaga yanda tai tsananin sanyi idanuwanta na sake cikowa da hawaye. Fuskewa ya sake yi ya nuna mata kofa dan shi kansa baisan dalilin da zai sakasa fita a cikin mutanen da Falaq ta tara masa ba ta tada kowa gidan ta daga hankalin kowa ana cirko cirko. Sake kallan jannah din yayi ta dago itama ahankali ta kallesa tana son magana amma batama san me zatace ba. Sake buga kofar Falaq tai hankalinta na sake tashi jin Daddynta shima shiru tace "Daddy are you ok? Kana ciki kuwa? Kar dai daddy shima baya nan ko wani abin ya samesa? Innalillahi bara na kira uncle" Juyawa tai da sauri zataje ta kirawo uncle dinta AZIZ din ya tako ya ya bude kofar bedroom din kai tsaye sbd kada ta sake tara mutane har nan din sbd na neman jannah wasa ne yanzune zata dagawa kowa hankalin rashin jinsa ko ganinsa. Dakatawa tai tareda juyowa da sauri ta kalli kofar dakin daya bude ba haske a cikinsa wutar ciki a kashe dan haka bataga Jannah datake bayansa ba shi kadai ta gani... Cikowa idanuwanta sukai da hawayen ganinsa dan hartashiga mafi munin tashin hankalin kwatanta idan wani abinne ya samesa dan haka da sauri ta iso gurinsa ta rungumesa hawayenta na saukowa na jin abinda ya danne kirjinta ya fada... Rungumeta yayi yana shafa bayanta zaiyi magana ta dan dago ahankali tana shaqar qamshin jannah dayake tashi a jikinsa, Bude idanuwanta tayi dakyau sai taga kaman jannah ce a bayansa, Baya tayi ahankali tana kallan bayansa tace "Daddy Jannah ake nema baa gangataba koina" Janyewa yayi gefe tareda bawa jannah din damar bayyana da kyau. Wata irin kunya da dana sani ne me tsanani ya rufe jannah din ta dago ta kalli Falaq data taho da sauri ta rungumeta tana cewa "Na dauka kin komawanki Zaadens ne shiyasa na damu dana sani na fara zuwa na fadawa daddy da kowa bazai damuba, I'm sorry Daddy, I'm jan" Komai bace ba ya juya yabarsu a tsaye ya komawansa bedroom dinsa ya rufe sbd baya buqatan fita idan ta fita kowa ya ganta sai kowa yaje ya nema guri ya kwanta. Barin palon sikai kowanensu na kasa kallan juna Falaq na jin tsananin rashin kyautawanta da takaicin kanta data kasa sanin ta girma inji mama. Jannah kuwa tsananin kunyar datake ciki ya sakata jin zazzabi na neman rufeta. Suna isowa main Living room su mama dake tsaye dukkaninsu hadda fadila ganin inda ta fito da kayan dake jikinta ya saka mama bata ce komaiba bare tsayawa jin abinda zai sakata jin kunya daga bakin falaq ta juya tabar palon ta nufi bangarenta ta shige ta turo kofa. Sayd ma ganin hakan ya juya shima yabar palon yana zuwa yacewa securities kowa y koma bakin aikinsa Mrs LIMBA din tana ciki. Fiddausi ma silalewa tayi ta koma dakinta cikin takaicin kanta data kasa tinanin ko jannah din na dakin Megidan gaba daya sai kawai ta daga hankalinta ta sanarwa Falaq duk da ba laifinsu bane tinda basu taba ganin ko zuwanta gurinsa ba bare tinanin hakan. #MAMUH ZAFAFA BIYAR KALBIM 500 mamuhgee A DUNIYATA 500 Huguma AJIYA A DUHU 500 Billyn Abdul KIRJIN ME HANKALI 500 Miss xoxo Pay at 0022419171 AccessBank Maryam sani gummi Shedan biya 09033181070 Or mtn vtu at 09032345899*_KALBIM_* _Mamuhgee_ 82 *UMMU_MAHNOOR LUXURIES* (Best luxuries shop) 08034469681 08135142610 Aslm Alaikm ina kuke masu neman luxuries na kayan alfarmar kece raini? Ina masu son su saka sitirar alfarma ta zamani ta manyan mata masu aji da zaa kalleki kallo daya asan sitirar alfarma e kika saka? Shin kunsan me ake nufi sa kayan asalin yan gayu da nuna gayu? Sitirar Alfarma kikeson sakawa? Sitirar da kike ganin manyan mata da ita? Sitirarda zakiyi gayun sallah dake da yaranki a dauka waje kikaje da kanki kika siyota? To kizo ga damarki ta sameki sbd UMMU_MAHNOOR LUXURIES ta kawo miki sauki har gida, Karkice se masu kudi ke iya siya har kema me yar dama zaki samu naki da saukin kudi kuma best quality da kalar zamani data yan gayu, Nidai Mamuh nace duk wadda ke son a buga gayun sallan bana da ita da 'yayanta to tazo gurin UMMU_MAHNOOR LUXURIES tai siyayyar sallanta harma zuwa gaba dan nasan zakuji dadi da fahimtar abinda nake fada akan kayanta💯💯 Abubuwan da zaki samu a gurinta with the best quality na wayayyun mata masu aji yan gayu sune; Atampopi Laces Shadda Materials Shoes Bags Veils Trolleys Jewellerys Oil perfumes Numbers 08034469681 08135142610 Handles Instagram @ummu_mahnoor_luxuries TikTok username @ummu_mahnoor_luxuries Facebook ummu_mahnoor_luxuries ********** Fadilah kuwa zubawa Jannah din idanuwanta tayi ahankali tana mata wani irin kallan dayake nauyaya zuciyarta, Wasu ruwane da suka gangaro ahankali daga gefen fuskanta a cikin towel din dayake nade da kanta suna gangaro ahankali zuwa gefen fuskan nata suna bin farar lafiyayyar fatarta har zuwa wuyanta sukai cikin rigarta wanda suka saka fadilan jin bugun zuciyarta na neman tsayawa sbd bata taba tinanin AZIZ LIMBA ashe yanada lokacin da zai bawa macen da bayaso harma ya iya bata kansa gabaki daya ya bata damar mallakarsa a matsayin Namijin dazai bata damar sanin ita din cikakkiyar mace ce, Kenan jannah ta amshe matsayin mace ta farko datasan waye Asalin AZIZ LIMBA, Jannah ta kwace mata matsayin dataso takawa a rayuwarsa, Taso kasancewa macen da zata fara saninsa, Macen da shima zai fara sani, Yaushe ma Jannah Zad tafara samun matsayi a gurinsa ne? Wucewa Jannah tai zuwa bedroom dinta batareda ta kalli inda Fadilan take ba dan ita batama lura da ita ba. Falaq ma bedroom dinta ta wuce aka bar Fadilan ita kadai tana jin kirjinta na tsananin nauyi da baqin cikin rashin kasancewanta macen da AZIZ LIMBA zai juya a hannuwa da jikinsa. Jannah na shiga bedroom dinta isa tayi bakin gadonta ta zauna tana dafe goshinta ahankali da hannunta tanajin kan na nauyi. Ta jima a hakan jikinta koina na dawowa daidai daga kakkarfan damqar data ringa samu daga garesa. Qamshinsa ne yake sake zuciyarta sukuni da tinaninsa dan haka ta miqe ahankali ta isa gaban dresser ta tsaya tana kallan fuskanta a jikin mirro ta zubawa lips dinta da sukai haske sosai sbd tsotsa ido ta lumshe tana jin qamshin bakinsa dayake kama dana mint da aka hada da raspberries yana dawo mata. Hand dryer ta kunna tana busar da kant ahankali tanajin dumin dryer din na ratsata jikinta amace. Har ta gama jikinta a mace yake ta kashe ta miqe tana kama gashin da band ta nufi gadonta ta haye ta kwanta tareda rufewa jikin duvet dinta qamshinsa dayake jikin kayansa dake jikinta yana ciketa koina ta rufe idanuwanta bacci na daukanta a natse. Washe gari kasa fitowa tai sbd kunya sai da Fiddausi ta shigo tukuna ta iya samun karfin fitowa gashi falaq ta tafi school. Gurin mama taje ta gaidata cikeda kunya da jin nauyi sedai maman ko kadan bata nuna mata ma ta iya tina abinda ya faru jiyanba janta kawai tayita yi da wata zancen tana sakata dawowa yanda suka saba abinsu. Fadilah ma bata iya fitowa ba tana daki zuciyarta da jikinta ba dadi duka. Mama hana jannah din komawa daki tai suka nufi dining hakama Fadilah fitowa tai breakfast suka hade a dining din.. Sayd ne ya shigo dining din shima yana fuskewa yana gaisawa dasu maman a sake sbd hana yanayin yiwa kowa nauyi. Yana zama suna kokarin farawa sai gashi ya sako kai dining room din sanye da Ash yadi me tsananin laushi da tsada daya nutsu a jikinsa fuskansa sanye da glass din versace dayayi masa wani irin kyau. Mamakin glass din fuskansa a gurin cin abinci mama tayi amma batai magana ba itama ganin kowa ya fuske. Gaidata yayi a natse kaman yanda ya saba yana zaunawa. Sayd ne ya fara masa barka da fitowa kafin Fadilah datake kallan Kyakkyawar fuskansa da lips dinsa masu wani irin kyau ta sauke ajiyan zuciya tukuna itama ta gaidasa a natse. Amsawa yayi batareda ya kalletaba.. Cup din tea me zafi ya dauka da Fiddausi ta zuba masa tin yana shigowa yakai bakinsa muryan Jannah a hankali cikin nutsuwa ta sauka a kunnen duk wanda yake gurin da cewa "Ina kwana?" Hadiye tea din me tsananin zafi yayi ta maqoshinsa har saida ya dan yi tari kadan ya dago idanuwansa ya kalleta kadan ya amsa a taqaice yanaci gaba da fara cin breakfast din da aka zuba masa na soyayyar farar doya datai laushi da sauce din hanta da qoda a hade da eggs sai tea da zuma. Breakfast sukeyi ba Hayaniya ba surutu sbd falaq bata nan dan haka tsit. Shine ya fara gamawa ya dauki tissue ya goge bakinsa ya miqe yabar dining din Sayd ma bayansa yabi. Suna ficewa daga dining din Jannah ta hadiye fries din daya kasa wucewa maqoshinta tin dazu ta daukan tea mara zafi sosai ta qarasa wutar dashi tana dagowa ahankali. Fadilah ma toshe mata maqoshi taji doyar wuyanta tayi dan haka ta dauki juice tasha da qarfi ta wuce ta ajiye cup din ta miqe tabar dining din. Mama kallan jannah tai cikeda kulawa tace "Ki nutsu kici abinci ki koshi kinji Jannah karki ji komai bakida matsala ko damuwar komai insha Allah" Kunya da sanyi ne suka rufeta lokaci daya ta dan saki murmushi me sanyi tana cewa "Thank you mama" Murmushi maman tai mata tana sake jin kaunar jannah din. A natse suka qarasa breakfast dinsu itada mama Suna gamawa duk da ba cikakkiyar lafiya ne da itaba amma ta fara dawowa daidai sosai. Tareda Fiddausi suka tattara gurin Fiddausi na bata labarin yanda mutuniyarta ta tafi school yau. Murmushi kawai takeyi tana taya Fiddausi aikin. ****Dr ken tinda asuba ya bugawa dr Abraham waya ya sanar dashi matarsa ba lafiya sosai dan haka ayau dole zai koma Germany. Cikin kulawa sosai Dr Abraham ya yadda da hakan, Daman yariga ya siya ticket tin a cikin daren dan haka koda yayi magana da Abraham kawai shiryawa yayi yafara jiran lokaci ya kusa dan ya tattara yayi Airport sbd jirgin yamma ne zai bi. Sayd kuwa aiki me tsafta yayi akan file din shi da fahad, An cire takardar qarshe ta Ummitah da har abada bazaiso hotonta a yanda take ba ya shiga duniya dan haka ya bada umarnin a ciresa. Abu na farko da Sayd ya fara triggering shine kiran Dr Abraha. Cikin nutsuwa ya dauka ahankali cikin nutsuwa Sayd ya gaisa dashi tareda sanar dashi personal person din AZIZ LIMBA ne Jannah Zad's Husband. Da girmamawa dr Abraham ya sake gaisawa dashi anan sayd ya sanar dashi suna buqatan File din Jannah zad sbd nasu likitocin zasu dubata sbd ko basa nan ya zamana nasu likitocin zasu iya cigaba da dubata. Shiru Dr Abraham yayi kafin yace ba damuwa yau zaizo limbas saiya hadu da likitocinsu zasu tattauna matsalarta da likitocin nasu zai musu handing over na komai. Ba damuwa Sayd yace yana kashe wayar tareda basa time na zuwan nasa. Suna kashe wayar Abraham ya nemo numbern Dzad ya saka kiransa. Dad kwata kwata baya cikin nutsuwa a yanzu damuwa ce da tashin hankali ninkin ba ninkin yake cikinsa sbd case din Anny ya girmama babu ta inda suke samun sauki a cikinsa, Babban tashin hankalinsu shine yanda Anny tafara kokarin tado maganar Sirrinsu wadda itace akai amfani da ita ta samu kanta a halinda take ciki yanzu. Tana cikin azaba me girma a prison da aka rufeta kafin shariar case dinta dan haka fiddata shine mafita garesu kafin a shiga court zata iya fadar abinda zai bude musu masifar datafi duka wainda suke ciki. Ta bangare daya gabaki daya AZIZ LIMBA ya janye daga jikinsu kwata kwata sai bibiyarsa Maheer da saleem suke sbd ya samu saka hannu a lamarin dan tsaf zai saka a sake Anny din. Wayar Dr Abraham ta sakasa sauke numfashi ahankali yace "File din Jannah ka tattarasa kabar Nigeria gabaki daya dashi, Acan dinma idan ka isa ka qonasa takarda daya bayan daya sbd a yanzu shi kadaine zai fita mu qarasa zamowa matacci, Anny barazana ce a yanzu ga wannan sirrin dan haka File dinne zai tabbatarda abinda duk zata fada dan haka ka tabbatarda babu file dinnan a doron duniya" Maheer dayake tareda Dad girgiza kai yayi Ahankali ya bude baki yace "No dad banajin fita qasar dashi shine mafita kawai ya kawosa yanzun nan ma anan cikin zaadens zamu qona komai a rufe case din tinda already ta riga ta samu zuciyar datake rayuwa da ita ba amfanin barin files din" Aminta da hakan dad yayi dan haka sukace kawai ya kawo file din. Dr Abraham kashe wayarsa yayi yana yin shiru sbd shima jin yayi yanason barin Nigeria kwata kwata sbd idan har da gaske maganar Anny zata iya tona asirin wannan file din to bayajin yana buqatan qara daukan lokaci a qasar dan haka Ken ya kira yaji yaushe ne tashin jirginsa ya sanar dashi karfe hudu ne. Time ya duba yaga akwai time sosai ma dan haka ya shima ticket ya siya ta waya ya fara hada kayansa, File din ya duba yaga bai gansa ba, Tsayawa yayi yana kokarin nutsuwa dan dubawa a natse. Sake fara dubawa yayi yaga bai gansaba, Fara yamutsa kaya yayi da karfi yana zubar da kayansa tas gurin neman file din amma babu... Zufa ne ya yafara jiqasa yana jin kansa na sarawa sbd bama abu me yiyuwa bane batan file dinnan a gidansa sbd tsowon shekaru kamar ransa haka yake kiyaye file dinnan. Rawa hannuwansa suka fara yafara kokarin zaunawa yana daukan wayarsa a rikice ya saka kiran wayar Maheer zad. Dauka Maheer din yayi yana jin haka kawai matsuwar a kawo file din su rufe komai da hannunsu. "I cant find the file anywhere" shine abinda Abraham ya fada zufa me tsananin gaske yana jiqasa. Maheer da maganar ta daki zuciyarsa cikin karfin hali yace "Pardon" Miqewa dr Abraham yayi yana sake jiqewa da zufa yace "I cant find the.... Bai qarasaba Maheer ya kashe wayar yana miqewa zufa na dan feso masa yace "Dad File din ya bata baya hannun Abraham ina buqatan zuwa na..... Zubewan Dzad dinne ya saka Maheer hadiye sauran maganarsa yana nufarsa cikin tsananin tashin hankali yana kiran sunansa. Abraham kuwa fitowa yayi da wani irin sauri ya nufi gidan Ken dayake kusa da nasa. Yana isa knocking ya fara cikin kokarin daidaita kansa amma hakan na neman gagara. Bude kofar ken yayi wanda yake shima ba cikin kwanciyar hankali ba kwata kwata so yake yabar qasar kawai. #MAMUH ZAFAFA BIYAR KALBIM 500 mamuhgee A DUNIYATA 500 Huguma AJIYA A DUHU 500 Billyn Abdul KIRJIN ME HANKALI 500 Miss xoxo Pay at 0022419171 AccessBank Maryam sani gummi Shedan biya 09033181070 Or mtn vtu at 09032345899*_KALBIM_* _Mamuhgee_ 83 *UMMU_MAHNOOR LUXURIES* (Best luxuries shop) 08034469681 08135142610 Aslm Alaikm ina kuke masu neman luxuries na kayan alfarmar kece raini? Ina masu son su saka sitirar alfarma ta zamani ta manyan mata masu aji da zaa kalleki kallo daya asan sitirar alfarma e kika saka? Shin kunsan me ake nufi sa kayan asalin yan gayu da nuna gayu? Sitirar Alfarma kikeson sakawa? Sitirar da kike ganin manyan mata da ita? Sitirarda zakiyi gayun sallah dake da yaranki a dauka waje kikaje da kanki kika siyota? To kizo ga damarki ta sameki sbd UMMU_MAHNOOR LUXURIES ta kawo miki sauki har gida, Karkice se masu kudi ke iya siya har kema me yar dama zaki samu naki da saukin kudi kuma best quality da kalar zamani data yan gayu, Nidai Mamuh nace duk wadda ke son a buga gayun sallan bana da ita da 'yayanta to tazo gurin UMMU_MAHNOOR LUXURIES tai siyayyar sallanta harma zuwa gaba dan nasan zakuji dadi da fahimtar abinda nake fada akan kayanta💯💯 Abubuwan da zaki samu a gurinta with the best quality na wayayyun mata masu aji yan gayu sune; Atampopi Laces Shadda Materials Shoes Bags Veils Trolleys Jewellerys Oil perfumes Numbers 08034469681 08135142610 Handles Instagram @ummu_mahnoor_luxuries TikTok username @ummu_mahnoor_luxuries Facebook ummu_mahnoor_luxuries *********** Kallansa Abraham yayi take yaga rashin kwanciyar hankali dayake tattare dashi dan haka ya shiga zargi me girma yace "Ina file din??? Wani irin kallo Ken din yayi masa cikin tsananin tashin hankali.da firgici ya bude baki yace "Wane file? "Jannahs" Wasu yawun wahala Ken ya hadiye yana sake kallan Abraham zaiyi magana Abraham din ya katsesa da cewa "Kana sane da girman hadarin dayake tattare da file din nan amma ka dauka? Ka manta adadin rayukan da muka salwantar ne a cikinsu? Ni da kai duka doctors ne munsan tsananin girman lefin abinda muka aikata akan aikinmu, Kare rayuka ne alkawarinmu amma nawa muka salwantar dan neman zuciyar da muke karban kudi a kanta? Mutanen nan sune suka tsayar damu muka zama abinda muke a yanzu? Da dukiyarsu muka gina kanmu, Kaman yanda suke biya ana kawo zuciyoyin mutane dan raya mutum daya a cikinsu to karka manta zasu iya komai akan kare sirrin dazai hana familyn duka zubewa, Idan kasan file din yana hannunka kai gaggawar bani mu bar qasar nan tare" Jajir idanuwan Ken sukai sosai yana jin kansa cikin masifar dabaisan meya kaisa shigartaba. Jin yake kaman bazai bar qasarba zaa iya kamasa dan haka baida lokacin batawa ya bude baki ya fadawa Abraham komai tareda kallansa yace "Idan kana son tsirar da kanka da rayuwarka bama career ba kayi shiru mu tattara mubar qasar nan sbd AY LIMBA bazai taba barin wanda ya raba Ummitah da rayuwarta ba" Dr Abraham wani irin shock ya shiga me tsananin girman gaske hannuwansa da qafafunsa suka hau rawa ya silale qasa ya fadi zaune. Ken dayake sake shida damuwa me tsananin gaske yana dafe kansa shima ya zauna yana dafe goshinsa na kansa ke tsananin sarawa. Shiru sikai cikin tsananin damuwa tsawon mintina kafin Abraham ya miqe yana kallan time ya fice daga gidan baice komaiba. Kayansa ya hada a akwati ya fito shima ken fitowa yayi suka tari mota batareda sun jira drivers dinsu ba dan baima san fatarsu ba yana dakin gate man din gidan kwance. Kai tsaye airport suka nufa kowannensu zuciyarsa na wani irin tsallen ganin sun daga daga qasar gaba daya. Jiniyar motocin jamian tsaro suka fara ji tako ina tana binsu. Ken ne ya juya yaga motocin kaman su ake bi dan haka ya kalli Abraham batareda kowannensu ya iya cewa komaiba suka fuske. Ken ne ya dan taba drivern yace "Pls we have a plane to catch can you speed up" Gudu driver ya qarawa motar wadda ta saka jamian tsaron qara gudu ana kokarin zagayesu. Me motar cikin mamaki ya rage gudunsa yana kokarin tsayawa sbd an riga an zagayesu harda bindigogi ana cewa su fito. Rintse idanuwa Dr Abraham yayi zufa na jiqasa ta ko ina, Dr ken kuwa kokarin waskewa yakeyi yana bude baki zaiyi magana aka saka masa bindigar cikin tsakiyar bakinsa wani qaton Dss na cewa kana magana zan fasa bakinka zuwa maqoshinka. Rawa jikin ken ya dauka ya hadiye maganarsa idanuwansa na ja. Dr Abraham kuwa yana fitowa motar sai hasken flashers suka fara gani tako ina ana daukan hotinansu. Da sauri aka shige mota dasu ana barin gurin yan media dake biye da jamian tsaron bin bayansu sukai da nasu motocin sbd dukkanin bayanan komai sun shigo hannunsu dan haka take ba bata lokaci aka fara yada labarin likitoci biyu da aka kama da laifin kashe mutane suna cire zuciyoyinsu dan siyarwa masu kudin da baa san me sukeyi da zuciyoyinb. Twinsting zancen su sayd sukai sbd baason saka sunnan jannah kai tsaye batareda case din ya isa inda ake son yakai dinba dan da akwai hali ma cire sunanta zaayi gabaki daya amma hakan bazai taba yiyuba sbd itace wadda akai komai akanta. Koda aka isa headquarters dasu Abraham tini maganar da sukai da safen a gidan ken ta iso nan batareda sun san ta yaya ba dan haka yan media ta ko ina daukansu akeyi wasu na jifansu daqyar aka samu wucewa dasu ciki. Yan media kuwa sai qara yadawa akeyi koina case din na yade koina. A daidai wannan lokacin Zaadens na kokarin ganin daidaituwar Dad sai kawai katsam labarin ya bayyanar musu a tv wanda ya sakasa Dad din qarasa rikicewa gabaki daya yana fita hayyacinsa. Hankali tashe suka kwashesa zuwa asibitin zaadens wadda akai gaggawar karbansa. Karban wayar mama Maheer yayi ya kashe sbd bayason taga komai, Saleem da shima kansa ke neman juyewa da Abinda aketa fada a labarai da kofofin yada labaran kasa fahimtar komai yayi dayaga yana neman rasa hankalinsa shima kashe wayoyinsa yayi, Ammar ma dashi aka taho asibitin duk da kan nasa haryanzu da saura amma ya dawo daidai a yanzu dan haka shima yana samun labarin shida Maheer neman zaucewa da tsananin tashin hankalin da ba damar nunawa sukeyi ga dad a kwance rai hannun Allah ga daddy mahmoud baya duniya ga anny a hannun huguma. Idanuwansu sunyi wani irin jajir kaman zasu zare kowa yayi shiru babu wanda baya cikin tsananin baqin ciki da damuwa da tashin hankali me tsananin girma a zaadens din. A daidai wannan lokacin Jannah na toilet tayo wanka ta fito ta shirya kenan ta zauna tana kunna qatuwar flat screen din dake dakinta hoton Abraham ne da ken suka bayyana da abinda ake zarginsu dashi. Wata irin mummunan bugawa kirjinta tayi ta gyara zamanta ahankali tana ajiye remote tana daukan wayarta ta saka kiran Dad dinta switch off, Wayar Mimi ta kira itama haka, Ta saleem ta kira shima kashe, Ta Maheer ta kira tana silenta bai daukaba, Wayar Ammar zad ta saka kira wanda koda kiran ya shigo wayar na hannunsa yana kokarin hada musu tafiya gabaki dayansu zaadens su bar qasar su koma inda suka fito. Kallan sunata da hotonta daya bayyana akan wayar yayi yana jin bugun zuciyarsa na sauyawa. Numfashi ya sauke ahankali kafin ya dauka a natse. Cikin damuwa tace "Lafiya kuke ku dukanku kuwa? Inata kiran kowa bana samu" Numfashi ya sauke ahankali tareda bude baki yace "Muna asibiti ne Dad ba lafiya" Miqewa tsayi daga zaunen datake zuciyarta na harbawa ba daidaiba tace "Dad? Meye samesa? Tin yaushe? Ina su Mimi? Meya samu dad din?? Take idanuwanta suka ciko da wasu irin hawaye masu tsananin dumi suna saukowa fuskanta sbd a rayuwarta yanda take tsananin kaunar mahaifinta bata hadasa da komai da kowa ba, Shine na farko a zuciyarta dayafi kowa, Tin tana yarinyarta ta taso da girmama tsananin girman kaunarsa a ranta, Kaman yanda yafi tsananin kaunarta fiyeda kowa da komai da rayuwarsa haka itama take tsananin kaunarsa fiyeda kowa da koman da kanta din. Ammar numfashi ya sauke me zafi yana bude baki zaiyi magana ta datse kiran tana miqewa ta sauya kayan jikinta zuwa doguwar riga ta zari key din motarta ta fice batareda sanin kowaba. Kasa bude mata kofa securities sukai suka kirasa suna kokarin sanar dashi motarsa ta iso gidan. Ana bude masa gate kafin ma motarsa ta sako kai ta fice gate din da gudu kawai tana barinsa da bin bayan motarta da kallo. Baice komaiba suka shigo kawai. Ko data isa kallo daya tayiwa familynta taji jikinta ya mutu da wani irin damuwa da tausayin kansu me tsanin gaske. Idanuwan Mimi gabaki daya sun kode sun jeme sbd kuka da damuwa, Saleem idanuwansa sun fada sosai gabaki daya ko abincin kirki ya dena ci a yanzu, Maheer duk jajirwa da jarumtarsa ya koma kalar tausayi damuwa da qunci tareda rashin mafita da madafa sun sakasa gaba. Ammar kuwa kai tsaye ya koma rabi lafiya rabi juyewan kai, Dukkaninsu sun rame kaman ba masu taqama da class da wayewa da arzikiba. A sanyaye ta iso ta zauna kusa da Mimi tana saka hannunta cikin na saleem daya bude mata hannunsa idanuwansa jajir. Shiru sukai babu me iya cewa komai sai saike ajiyan zuciya da numfashi kawai sukeyi. Ammar kuwa cigaba yayi da hada musu shirin barin qasar. Acan asibiti ta wuni sai dare ta dawo gida shima sbd Mama sunzo tareda falaq da Fiddausi ne sun duba dad din sai suka koma tare. Koda suka dawo gidan shigewa tai zuciyarta kwata kwata ba dadi tai wanka daqyar taci abincin da mama ta takura mata taci tai sallolinta ta kwanta. Kwana tai tana yiwa mahaifinta addua sbd batasaniba ko zata iya rayuwa idan ta rasa mahaifinta. Tashin hankalin da zaadens ke ciki na Dad dayake sake nisa ya saka kwata kwata suka aje maganar kama su Abraham da akai kokarin barin qasar sukeyi da dad dinma gabaki dayansu. Su Abraham kuwa kwana sukai ana basu azabar data wuce hankali sbd sun kasa magana hakama har lokacin LIMBA bai fito ya shiga cikin case dinba kaman yanda basu bada evidence gaba daya ba wanda zai nuna zaadens na ciki sbd so yake su fada da bakinsi su waye sukewa aiki. Washe gari Dad ya farfado amma yana cikin matsanancin ciwo har lokacin, Karfe goma da rabi AZIZ LIMBA ya iso asibitin wadda yayi alkawarin bazata qara sati batareda anrufeta an konataba. Dukkanin Zaadens na ganinsa zuba masa idanuwa sukai harya qaraso suka gaisa dashi da sauran girmamawa. Mimi juyawa tayi ta fice a natse jikinta a sanyaye bayan sun gaisa, Saleem ma bayanta yabi sbd ganin bata iya tsayuwa daidai. Ammar da hannuwansa suka fara rawa zuciyarsa na wani irin tsalle da tafasa har cikin kwakwalwansa ya kalli AZIZ din ya bude bakinsa dayake zafi kaman zai fidda wutar datake neman kashesa a zuciyarsa yace "Kanason qarasa shima kaman yanda kayiwa Daddy mahmoud? Tinda ka shigo rayuwarmu alkhairi ya dena shigowa cikinta, Meye laifin ko illan da mukai maka kake bibiyar rayuwarmu kake illata mu??? Dago idanuwa AZIZ yayi Ahankali ya saukesu akan Ammar din suna sauyawa ahankali zuwa ja me bayyanarda tsananin ciwo da daci tareda fushi da tsana me karfin gaske ya bude baki yace "Kana buqatar sabon sani ne bayan wanda kake dashi na ni din waye? Kana buqatan sake sanin fuskan waye akan tawa fuskan? Kana buqatan sake sanin fuskan da kuka kwantar kuka fedewa kirji kuka zarewa rayuwa dan raya wata rayuwar?" Wata mummunan faduwa gaban Maheer yayi yana kallan Ammar da sauri kafin ya kalli AZIZ din wanda idanuwansa sukai jajir hannuwansa na wata irin rawa. Dad dayake kwance shima cikin azabar ciwo bude idanuwansa yayi da karfi akan AZIZ numfashinsa na neman sarkewa. #MAMUH ZAFAFA BIYAR KALBIM 500 mamuhgee A DUNIYATA 500 Huguma AJIYA A DUHU 500 Billyn Abdul KIRJIN ME HANKALI 500 Miss xoxo Pay at 0022419171 AccessBank Maryam sani gummi Shedan biya 09033181070 Or mtn vtu at 09032345899*_KALBIM_* _Mamuhgee_ 84 *UMMU_MAHNOOR LUXURIES* (Best luxuries shop) 08034469681 08135142610 Aslm Alaikm ina kuke masu neman luxuries na kayan alfarmar kece raini? Ina masu son su saka sitirar alfarma ta zamani ta manyan mata masu aji da zaa kalleki kallo daya asan sitirar alfarma  e kika saka?   Shin kunsan me ake nufi sa kayan asalin yan gayu da nuna gayu? Sitirar Alfarma kikeson sakawa? Sitirar da kike ganin manyan mata da ita? Sitirarda zakiyi gayun sallah dake da yaranki a dauka waje kikaje da kanki kika siyota? To kizo ga damarki ta sameki sbd UMMU_MAHNOOR LUXURIES ta kawo miki sauki har gida, Karkice se masu kudi ke iya siya har kema me yar dama zaki samu naki da saukin kudi kuma best quality da kalar zamani data yan gayu, Nidai Mamuh nace duk wadda ke son a buga gayun sallan bana da ita da 'yayanta to tazo gurin UMMU_MAHNOOR LUXURIES tai siyayyar sallanta harma zuwa gaba dan nasan zakuji dadi da fahimtar abinda nake fada akan kayanta💯💯 Abubuwan da zaki samu a gurinta with the best quality na wayayyun mata masu aji yan gayu sune; Atampopi Laces Shadda Materials Shoes Bags Veils Trolleys Jewellerys Oil perfumes Numbers 08034469681 08135142610 Handles Instagram @ummu_mahnoor_luxuries TikTok username @ummu_mahnoor_luxuries Facebook ummu_mahnoor_luxuries *********** Maheer ma matsanancin shock dayafi na Dad ya shiga bakinsa na bushewa, Shi kansa Ammar dayake tinanin hakanne yasan waye AZIZ LIMBA din jin maganar daga bakin AZIZ din sai daya mugun girgizasa ya kallesa da sauri idanuwansa na yin jajir harda cikowa da wasu hawaye masu tsananin karfi. Dad kirjinsa tsananta ciwo yayi idanuwansa sukai jajir ya rintsesu ahankali zafafan hawaye masu tsananin zafi na gangaro masa, Kallansu AZIZ din yayi da jajayen idanuwansa daya bayan daya tsananin ciwon dayake shimfide a zuciyarsa yana tasowa, Akan Dad da idanuwansa ke tsiyayo hawaye masu tsananin ciwo yayi kafin ya saka hannuwansa biyu ya kamo wuyan rigarsa ya dagosa da karfi ya jijjigasa yace "Kana hawayene sbd yarka datake hannun wanda bazai taba yafe abinda kukaiwa tasa 'yar ba? Wannan radadin dakake ji a zuciyarka ko kadan baiyi zafi da ciwon wanda kuka sakamin ba" Wurgi dashi a gadon AZIZ yayi yana dawo da kallansa kan Maheer daya isa da sauri ya tare Dad daya fado gadonsa numfashinsa na neman yankewa sbd zuciyarsa dake neman bugawa da tashin hankali yace "Jinin Limbas a tsarkake yake baya da tsatsa ko daya, Bana bata hannuwana da imanina da jinin kowa amma lalata rayuwarku da tabbatarda kun nema kisan kanku da kanku shine abinda bazan taba barin qasar ba saiya tabbata, Ban taba so ko kaunar sadakar da kuka ban ba, Amma bazan taba dawo muku da itaba saina mayarda ita masu aikin gidana ma sun fita daraja da kyan gani" Ammar ne yayo kan AZIZ din cikin tsananin bacin ran da ko gani bayayi zai miqa hannunsa ya kama wuyansa Wani lafiyayyan marin daya sakasa juyawa gefen Maheer baya gani sosai ya sauka fuskansa daga Sayd wanda yasha gabansa a hankali yana masa kallan tsana me tsananin gaske, Sake juyowa Ammar din yayi yana fita hayyacinsa zai sake nufar AZIZ Sayd ya sakar masa wani mahaukacin marin tareda kama hannunsa ya sake sakar masa wani marin idanuwansa ba rufewa shima zuciyarsa na tafasa tako ina jin yake ayau da suka fuskanci juna a matsayin su din babu boyo kaman zai iya kashe Ammar yakeji sbd radadi da tsana me karfi ce yake dannewa da boyewa tsawon lokaci amma banda yau. Kasa dena tasowa Ammar yai sbd gabaki daya ya fita hayyacinsa AZIZ yakeson shaqewa ya rabasa da duniya ko zasu samu salamar rayuwarsu daya riga ya lalata masu su duka kaf zaadens. Sayd da shima nasa idanuwan suke a rufe da zuciyarsa duk motsi daya idan Ammar yayi na yunqurin matsowa mugun naushin dayake fasa hancinsa yake sakar masa yana jin zuciyarsa na kasa samun sassaucin abinda yake ji ko kafan. Maheer dayake riqe da Dad dake neman rasa ransa hawaye ne masu tsananin radadi da ciwo shima suka gangaro masa ganin yanda hancin Ammar ke fidda jini. Juyawa AZIZ ya fice sbd shima zuciyarsa gap da sakasa hawayen tsananin ciwon dayake ransa.... Sayd kuwa saida ya tabbatarda Ammar ya zube qasa yana neman taimako kafin ya juya ya fice daga dakin hawayen d suka cika idanuwansa suna zubowa kan fuskansa ahankali. Barin asibitin sukai, Suna ficewa Maheer ya buqaci likitoci suyi gaggawan zuwa ga dad, Ammar ma gaggawar ficewa akai dashi daga dakin ana wucewa dashi inda zaa dubasa, Mimi kallo daya taiwa Ammar ta kusa yanke jiki ta fadi Saleem yayi saurin riqeta yana shiga tsananin mamaki da tsoron meya faru shima, Jamian tsaro likitocin zasu kira Maheer ya hanasu yana cewa su barshi issue din cikin gida ne. Hankalinsu dawowa yayi kan Dad da aketa kokarinsa ceto rayuwarsa datake nisa, Ammar ma aka gyarawa fuska duk bandage dawowa yayi dakin suka zauna zaman jimami da qunci sbd babu me iya magana idan ba ganin sukai Dad ya farfado ba, Maheer wasu hawaye ne masu zafi ne suka ganganro masa ahankali yana jin zuciyarsa na neman mutuwa, Idan dad bai tashi ba baisan ta ina zai fara rayuwarnan ba da sauran familyn da nauyinsu zai rataya akansa baida mai jagoransa, Ta ina zai fara fuskantar babbar matsalar da suka aikata su da yawa a wayi gari ace shi kadai ne zai fuskanceta sbd Ammar dai ya riga ya samu tabin kan da ba lallai ya karba hukuncin komaiba, Tayaya zai iya kubutar da jannah daga AZIZ shi kadai? Innalillahi wainna ilayhi rajiun"""' shine abinda zuciyarsa ke maimaitawa yanajin kaman zuciyarsa zata fashe. Mimi bata iya magana a yanzu karfinta ya qare tas tayi weak sosai batajin dadin zuciyarta ko kadan, Saleem ma kusan baida abin cewa ko tambaya sbd komaima a yanzu kamar baida amfani, Dukkaninsu qasar suke son bari su koma inda suka fito rayuwar zatafi musu dadi acan, Zasu bude sabuwar rayuwa su sake gina sunansu cikin kwanciyar hankali da Aminci. Ganin jikin Dad din yana sake nisa sai kawai Maheer ya kira jannah daya san dad din zaiso ace ya bude ido yayi mata ganin karshe. Koda Maheer ya sanar da ita ana sallar ishai lokacin dan haka sallar ta samu kawai tayi jikinta na dan rawa zuciyarta na wani irin rawar tsananin tsoro da tashin hankali. Ko mama bata tsaya fadawa ba ta fita hannuwanta na wata irin rawa. Ganin yanayinta ya saka falaq hanata driving tace suje da driver su kaita tinda dad din baya nan. Bata musa ba sbd bata cikin cikakkiyar nutsuwarta matsanancin tsoro ne ya rufeta sbd batasan tina mutuwa akan mahaifinta da shine rayuwarta. Tausayinta sosai falaq takeji sbd tasan irin tsananin so da kaunar datakewa Daddynta shi Jannah kewa Dad dinta dan haka kwatanta rayuwa babushi abune da shi kadai zai iya zarar da kai. Koda suka isa asibitin falaq bata fita motar ba ta bari jan din ta tafi ita kadai sbd ta fara ganinsa ta samu nutsuwa tukuna. Jannah na isa dakin a sanyaye ta bude ta shigo dukkaninsu suka dago jajayen idanuwansu da duk suka jeme suka zuba mata. Sanyi qafafunta sukai ta tako ahankali hawayen cikin idanuwanta na saukowa ta nufi gadon Dad din wanda yake kwance kamar ba rai a jikinsa yayi mummunan jemewan data sakata rintse idanuwanta tana zaunawa bakin gadon ta dora hannunta akan nasa tana fashewa da kuka mara sauti. Tsit dakin yayi kowa ciwon ransa na qaruwa kukanta na ratsa kunnuwansu. Mimi ce ta bude baki Ahankali batada ko wani karfi sosai ciwon dayake cin zuciyarta na bayyanuwa cikin mutuwar jiki tace "Mahaifinki bai hada soyayyarki data komai da kowa ba amma ayau mijin da kika zaba kikace shi kikeso wanda a hakan mahaifin naki ya zabi farin cikinki akan familynsa shine yake neman neman ganin bayan mahaifinki da ahalinki, Me ahalinmu sukai masa dayake neman ganin bayanmu? Wane irin miji ne zai cakumi mahaifin matar dayake aure bayan yasan baida lafiya sosai??? Jannah me kikeyi da wannan mijin? Me zakiyi da miijin dayake neman rayuwar ahalinki? Kalli fuskan Ammar kiga abinda yayi masa, Wannan shine mijin da zuciyarki ta zabar miki akan ahalinki da suka zabeki fiyeda rayukansu? Wannan shine sakamakon soyayyar da mukai miki tin kina yarinya? Dago jajayen idanuwanta tai cikeda mamaki da tsoro harma da fargaba me tsanani tana kallan Mimi kafin ta maida kallanta kan fuskan Ammar da sai a lokacin ta lura nade take da bandage mummunan duka ne a fuskan ba kyan gani. Waya Ammar ya fidda ya nuna mata hotinan da yayiwa AZIZ a lokacin daya shaqo Dad ya zubar. Mummunan faduwa gabanta yayi ta dago cikin slow ta kalli Maheer wanda idanuwansa suke jajir ya kasa kallanta. Kan Saleem ta maida kallanta wanda ya saukar da idanuwansa da sukai jajir shima a hankali yana jin ciwo da radadin abun har qasan zuciyarsa. Wani irin nauyi me girman gaske taji yana danne kirjinta ta juya ta kalli mahaifinta hawayen baqin ciki na gangaro mata tareda da jin soyayyar AZIZ LIMBA na sauka daga zuciyarta ahankali tana zubewa. Ammar kuwa bude bakinsa dayake rawa sosai kamar me koyan magana sbd kansa dayake a juye tin dazu da azabar duka ta tayar da ciwonsa yana bubbuga kansa da hannunsa idanuwansa na sake rinewa da ja yace "AZIZ LIMBA makashi ne, Shine ya kashe Daddy mahmoud, Shine yake kashe kowa, Shine ya kama su Abraham, Shine yakeson kashe dad, Idan ya kashe dad zai kashe kowa, Kema jannah yace saiya kashe ki, Zai kashe kowa, Bazai dena ba saiya kashe kowa dayake zaadens sbd Qanwarsa, Qanwarsa ce a kirjin jannah, Qanwarsa ta mutu, Yace saiya kashe kowa, Ya fada da bakinsa....... Shiru sukai dakin ya sake daukan shiru maganganun Ammar na futa hayyaci ne kawai suke tashi ahankali kuka na zuwar masa. Maheer zuciyarsa ta gama saddakar da komai vazan iya hana ammar maganar data saka su mimi shiga tinani ba sbd komai dai yazo karshe da alama. Mimi gabaki daya hawaye take tsiyayarwa na baqin cikin jin Ammar na magana a zare basuda abinda zasu iya yi, Saleem ma baqin ciki da ciwon zarewan Ammar din ne ya hanasa fahimtar abinda Ammar din yake fada. Falaq dake tsaye kofa isowanta kenan taji dukkanin maganar da Ammar yake fada akan Daddynta wata irin mummunan bugawa kirjinta yayi kafafunta suka dauki rawa zuciyarta na kasa dauka ta shigo idanuwanta na cikowa da hawaye masu zafi tace "Daddyna ba makashi bane bazai kuma taba zama makashinb insh......." Ammar da dukkanin jikinsa ke rawa kanta yayi idanuwansa na rufewa ya shaqota yana bugata da bango da karfi bakinta ya fashe da jini ya saka hannuwansa biyu ya shaqeta yana cewa "Saina kashe AZIZ LIMBA, Saina kashesa saina kashesa kaman Ummitah, Saina kasheki, Ai kene AZIZ LIMBA...... Mimi,Saleem da maheer da tsananin tashin hankalin dayafi wanda suke ciki sukai kansa suna kokarin kwace Falaq wadda bakinta ke jini sosai tana kokarin riqe numfashinta dake kokarin saka zuciyarta dena bugawa sbd bugun zuciyar ya sauya sosai zuwa yanda baa so gashi sosai aka tabbatarwa limbas takai matikin da baaso ta sake samun matsala. Jannah zubewa qasa tai tana fasa wani irin kuka me tsananin ciwo da qunci kamar zuciyarta zata fashe. #MAMUH ZAFAFA BIYAR KALBIM 500 mamuhgee A DUNIYATA 500 Huguma AJIYA A DUHU 500 Billyn Abdul KIRJIN ME HANKALI 500 Miss xoxo Pay at 0022419171 AccessBank Maryam sani gummi Shedan biya 09033181070 Or mtn vtu at 09032345899*_KALBIM_* _Mamuhgee_ 85 *UMMU_MAHNOOR LUXURIES* (Best luxuries shop) 08034469681 08135142610 Aslm Alaikm ina kuke masu neman luxuries na kayan alfarmar kece raini? Ina masu son su saka sitirar alfarma ta zamani ta manyan mata masu aji da zaa kalleki kallo daya asan sitirar alfarma e kika saka? Shin kunsan me ake nufi sa kayan asalin yan gayu da nuna gayu? Sitirar Alfarma kikeson sakawa? Sitirar da kike ganin manyan mata da ita? Sitirarda zakiyi gayun sallah dake da yaranki a dauka waje kikaje da kanki kika siyota? To kizo ga damarki ta sameki sbd UMMU_MAHNOOR LUXURIES ta kawo miki sauki har gida, Karkice se masu kudi ke iya siya har kema me yar dama zaki samu naki da saukin kudi kuma best quality da kalar zamani data yan gayu, Nidai Mamuh nace duk wadda ke son a buga gayun sallan bana da ita da 'yayanta to tazo gurin UMMU_MAHNOOR LUXURIES tai siyayyar sallanta harma zuwa gaba dan nasan zakuji dadi da fahimtar abinda nake fada akan kayanta💯💯 Abubuwan da zaki samu a gurinta with the best quality na wayayyun mata masu aji yan gayu sune; Atampopi Laces Shadda Materials Shoes Bags Veils Trolleys Jewellerys Oil perfumes Numbers 08034469681 08135142610 Handles Instagram @ummu_mahnoor_luxuries TikTok username @ummu_mahnoor_luxuries Facebook ummu_mahnoor_luxuries *************** Ahankali Dad idanuwansa suka bude sika sauka akan ahalinsa da suke cikin mummunan yanayi anata kokarin cire falaq a hannun Ammar wanda ya qarasa haukacewa gabaki daya ya koma asalin cikakken mahaukaci, Kuka sosai Mimi takeyi tana jansa a jikinta amma sam yaqi banbaruwa, Jannah datake kuka mai tsananin gaske jin take inama ta bude ido taga duka wannan rayuwar da sukai tin farkon dawowansu Nigeria mafarki ce, Inama ta koma lokacinda take cikin ciwonta tayi jinyarta cikin Aminci ta tafi ta huta, Maheer cikin tsananin zafi da tashin hankali ya sakarwa Ammar din wani mummunan marin daya sakasa faduwa shi da Mimi datake rugume dashi ta baya. Saleem ne cikin tsananin sauri ya tare falaq ta zata zube qasa babu numfashi a jikinta ko kadan. Da sauri jikinsa na tsananin rawa ya fito da ita zai nufi emergency da ita latif dayake mota idanuwansa suka sauka akansu da tsananin firgici ya futo ya nufosu yana cewa "Meya sameta???? Akan jinin dayake fuskanta da kayan jikinta idanuwansa suka sauka wata mugun firgici ya shigesa baisan lokacinda ya kwatota daga hannun saleem dinba yana nufar mota da ita cikin tashin hankali da tsoro me tsananin gaske. A rikice ya figi motar ya nufi gida kaman zai tashi sama sbd yasan ganganci ne zaiwa AZIZ LIMBA barin a duba falaq din asibitin zaadens. Koda ya iso gidan cikin matsanancin tashin hankali yayi ciki ya kira mama da Fiddausi cikin tashin hankali suka fito.. Fiddausi kallo daya taiwa Falaq take jikinta ya dauki rawa tayi kanta tana tallafo ta, Mama kuwa a rikice ta kallesa tace "Accident kukai? Meya sameta? Innalillahi wainna ilayhi rajiun, Ku kuramun AZIZ da sauri a waya kar naga baqar rana yau" Kokarin fiddo da falaq din mota ake aka wangale gate Dukkaninsu mayar da kallansu kan gate din sukai ganin motar AZIZ ce gaban Latif yayi mummunan faduwa. Sayd parking yayi yana kallan su maman. Shi kansa AZIZ ganinsu harabar gidan duka ya sakasa fitowa yana kallansu kafin kowa ya motsawa idaniwansa suka sauka akan Falaq da Fiddausi da fadilah suka fitar kamar wadda tai hadarin mota. Miqawa Sayd wayoyin hannunsa yayi yana isa gurin kai tsaye ya karbeta gabaki dayanta yana cewa "Meya sameta???? Cikin wani irin mummunan yanayin daya sake saka jikin kowa sanyi. Mama a rude tabi bayansa tana cewa "Accident sukai" Sayd kuwa wayarsa y fidda cikin tsananin sauri ya kira likitoci yanace maza maza ana buqatansu. Dukkaninsu ciki suka dungumo hankali tashe. Babu bata lokaci su dr Ashir suka iso tareda nurses da komai na buqatan taimakon gaggawa.. A wannan lokacin ne Latif ya tako ahankali cikin damuwa me tsanani ya sanar dashi ba ba Accident bane daga dakin zaadens kome ya faru. Rintse idanuwansa da sukai jajir yayi Ahankali wani irin abu na gangarawa kirjinsa ya danne masa. Abu dayane yazo kansa Ammar ne ya taba masa 'ya.... Sabuwar tsanar zadeens din yaji tana gaurayesa wadda take kewaya dukkanin jinin dayake yawo jikinsa, Duk taimakon dasu dr Ashir zasu bata sun bata sedai bugun zuciyarta be dawo yanda akesoba da alama ta riga ta shiga stage din da baa so, A yanzu akwai hope qalilan idan har bazata sake bugawan zuciya ba sbd tana sake samun attack shikenan komai ya lalace kodai a mata dashen zuciya kokuma ayi hakuri a jira lokacinta kawai. Wannan zancen da dr Ashir ya koro masa bayan sun mata wasu irin gwaje gwaje har kusan asuba shine ya tarwatsa dukkanin kuzari da zuciyar wanda yake limbas sbd maganace da akai gaban kowa. AZIZ din kasa riqe kansa yayi ya zube qasa a gaban likitan yana cusa kansa cikin qafafunsa idaniwansa n wani irin radadin daya saka mama fasa kuka mai tsima zuciya sbd bata taba tinanin zasu iya rasa jinin da Ummitah tabar musu a duniya ba, Rasa falaq shine rasa jinin Fatimanta a duniya kwata kwata sbd AZIZ bazai taba rayuwa ba idan ya rasa Falaq wadda itace abinda ta rikesa da yanzu ya dade da mutuwa a nakasashe mara hankali. Sayd kuwa gurin mahaifinsa ya tafi ahankali ya silale gabansa ya zauna ahankali baisan lokacinda wani irin kuka me sanyi yazo masa ba, Kaunar yarsa a jininsa yake wadda rasata rasa AZIZ ne wanda yakewa kallan jininsa da shima zai iya shiga mummunan hali idan ya rasa. Fiddausi ma kuka takeyi sosai sbd tamkar yar data haifa takejin Falaq kaunace a tsakaninsu me girma da tsafta, Dik karfin halin fadilah ma sanyi jikinta yayi cikeda tausayin ahalin gidan da falaq din kanta data koma abin tausayi lokaci daya tayi fayau da haske sosai sbd matsalar zuciyar a take take janye albarka jikinta.. Tsit gidan yayi kaman gidan mutuwa sbd kowa na cikin tsananin dacin zuciya da qunci, Ko securities da masu aiki gabaki daya kowa jikinsa a sanyaye yake. Daman kwana zaune akai gidan likitoci na kan Falaq din. ***acan asibiti suma kwanan zaune sukai sbd Ammar daya rikice hakama Dad ba sauki ko kadan ga Mimi zuciyarta ta fara kasa dauka, Maheer na ya zaunar da ita ya sanar da ita qasar zasu bari gabaki dayansu. Shiru tayi zuciyarta na wani irin sanyi da ciwo duk a lokaci daya wanda a wannan karan batajin soyayya zata hanata bude idaniwanta ta tsaya tareda familynta da sukai sacrificing komai akanta, Numfashi me zafi ta sauke ahankali tana hadiye wani irin daci da ciwo ta kalli Maheer tace "Na Amince zan biku mu tafi bazan sake waiwayan baya ba" Dad ne ya sauke numfashi ahankali cikin ciwo na jin dadin abinda ta fada, Maheer ma numfashin ya sauke yana jin samun sanyi da saukin nauyin kirjinsa. Hudu na yamma likitoci da nurses din mahaukatan daya gayyato daga lagos jirginsu ya sauka daga airport kai tsaye motocin asibitin Mahaukatan nan abuja ce tazo ta daukesu tareda motar jamian Drugs da babu me alamar yasan imani a acikinsu suka isa asibitin Zaadens. Suna isa dakin da Ammar yake kwance an dauresa a gado abi na farko wani mahaukacin mari Wani Dan drug ya fara kashesa dashi wanda ya saka haukarsa daukewa ta wucen gadi. Motocin police ne kusan guda biyar suka iso asibitin take guri ya cika aka hargitse. Wani mummunan daurin azaba akaiwa Ammar kamar goro yana ihun tsananin azabar da bai taba ji ba aka fito dashi tareda takardar asibitin mahaukata zaa kaisa ta lagos. Duk tsananin ciwon dad saida ya tashi daqyar suka fito dukkanin familyn suna roko da neman taimako cikin mummunan tashin hankali da fita hayyaci. Maheer ayau kuka yakeyi kaman mace a gaban tarin mutane amma wani ball da akai dashi saida ya fasa goshi. Dad ma kuka yakeyi sosai kirjinsa na tsananta ciwo. Mimi kuwa yanke jiki tai ta fadi saleem yayi kanta. Jannah kan maheer tayi tana goge masa goshinsa daya fashe da hannun rigarta idanuwanta jajir. A dakin da dad yake aka kwantar Mimi dan haka dukkaninsu sunyi shiri zuciyoyinsa na ciwo da tarin baqin cikin daya rufesu, A rayuwarta soyayyar AZIZ LIMBA itace mummunan kaddarar data afkowa rayuwarta harta tarwatsa mata family ayau sike cikin mummunan halin dasuke buqatan dauki. Tayi danasani da baqin Kamuwa da soyayyar wanda bai taba sonta ba qarshen iyayenta kawai yakeso batareda laifin komaiba, A yau tayiwa kanta alkawarin ta hakura da rabuwa da aurensa, Idan ita yar halak ce zata cire soyayyarsa har abada bata buqatansa... Miqewa tayi ahankali ta fice daga dakin taba jan kafafunta daqyar. Gate ta nufa idanuwanta jajir ko gani sosai batayi ta tari mota ta shiga ahankali tana rufe idanuwanta bayan ta sanar dashi idan zai kaita. Ahankali ta miqa hannunta ta dora akan zuciyarta dake bugawa da tsananin ciwo da quncin datake jin yana sake ciketa tako ina. ko data iso gidan security da sauri suka bude mata gate ta shigo tana tafiya cikin quncin daya rufe idanuwanta. Ciki ta shigo babu kowa a main palo sai Fiddausi data ganta ta qaraso cikin tsananin sanyi tana mata sannu da zuwa amma sam Jannah batajinta sbd nisan datai a cikik matsanancin qunci da tinani me ciwo. Kai tsaye dakin Falaq ta isa ta taddata kwance kamar wadda tai shekaru a kwance. Silalewa tai ahankali bakin gadonta tana fasa wani irin me tsuma zuciya da tsananin ciwo da radadin rabuwar da zatai da ita har abada batason su sake haduwa sbd haduwansu ba alkhairi bane garesu su dukan gwara kowa yayi rayuwarsa. Kukane tayi sosai wanda baida sauti ko kadan zuciyarta na tsananin ciwo tsawon lokaci kafin ta miqe ko gani batayi sosai ta fice daga dakin sedai batasaniba Falaq din ta bude idanuwanta itama Hawaye takeyi sosai batareda ta motsa ba sbd tsananin qunci da azabar ciwo take ji itama wanda yake sakata jin tsoron kamar mutuwa zatai. Tana fitowa kai tsaye palonsa ta nufa ta bude kofar ta shiga daidai fitowansa idaniwansa sun fada sosai a lokaci daya sbd tsananin damuwa da tsoron dayake bayyane a yanayinsa na tsoron rasa 'yarsa da itace rayuwarsa. Tsayawa sukai suna kallan juna ahankali tsana na tasowa ahankali tana rufe zazzzafar soyayyar dake qasan zuciyoyinsu, Ahankali ta tako ta tsaya gabansa ta bude baki tana kallan cikin idaniwansa tace "Meyasa? Why? Mun cancanta hakan daga gareka ne? Sbd zuciyana ta mutu akan soyayyarka ne ka zabi hukunta iyayena da yan uwana akan laifin daba nasu ba? Duka soyayyar danake maka ne ta jawo wannan? Wasu hawayen tsananin radadin zuciya ta hadiye ahankali tana cewa "AZIZ LIMBA kaje nayi freeing dinka daga Soyayyar da kake cutatar da ahalina akanta, Na cireka daga zuciyata bazan qara sonka har abada, Sadakata aka baka ayau ina rokonka ka jefar da sadakar da bakaso ka bani yancina na maka alkawarin har abada bazaka sake sakani a idaniwanka ba zan tabbatarda hakan sbd ni kaina bazan taba son sake saka ka idaniwanaba....... Jajir idaniwansa sukai tiririn dayake cin zuciyarsa na tafasowa ya jefa mata mummunan kallo tana ficewa daga rayuwarsa gabaki daya ya dago file din dayake hannunsa nata wanda zai bawa Sayd ayau a saki duniya tasan su waye zaadens ya jefa mata a fuskanta takardun duka watse gabaki daya a qasa. Cikin tsananin tsanar familynta datake juyewa harda ita yace "Yaushe kika samu bakin tambayar why? A zaadens babu me darajar da zai tambayeni na amsa harke din, Ki dena tambayar auren dayake kanki sbd tin farko ban daukeki mata ba kuma bazaki taba zama matar dani AZIZ LIMBA zan ambata da matataba, Amsa kikeso na abinda familynki sukai? Kije ki tambayesu zuciyar waye a kirjinki take harbawa? Ki duba ga takardu nan rai nawa suka kashe kisan gilla kafin su kashe mace me tsohon cikin da zuciyarta take bugawa yanzu haka a kirjinki, UMMITAH ABDULAZIZ LIMBA shine sunan, Shine sunan mahaifiyar data haifi Falaq, Shine sunan Qanwa kuma jinin AZIZ LIMBA daya dayake da ita a duniya da bustards dincan suka kashe sbd a raya waye????? Ke sarauniyar Zaadens da ranta yafi na kowa, Ummitah data raye da yarta da mijinta Sayd a cikin Aminci badan ke ba, Badan keba da yanzu Falaq tana raye tareda mahaifiyarta, Da yanzu yaya na yana tareda qanwarsa daya taso baida kowa sai ita, Itace rayuwata,itace gabaki dayan AZIZ LIMBA amma suka farka kirjinta suka rabata da zuciyarta sbd son zuciya and kin samu daman tambayar me sukai? Sarewa kafafun Jannah sukai cikin matsanancin tashin hankalin daya saka zuciyarta bugawa ta durqushe tana dafe kirjinta sbd tsananin azabar gaske takeji idanuwanta na neman rage gani. Falaq datake tsaye bakin kofar cikin rashin karfin jiki kunnuwanta suka ji mata kalaman da suka juya duniyarta lokaci daya jini ya fara biyowa ta hancinta ahankali kafin tausayi wani motsin harta bakinta yafara fitowa.... Mama ma data biyi bayan falaq din dataga wutowarta mutuwar tsaye tayi da abinda kunnuwanta suka ji mata amma ganin yanda jini yake fita baki da hancin Falaq tana yanke jiki ta fadi ya sakata ambatar sunan Falaq din cikin amon daya saka AZIZ kallan kofar yana yi kan falaq cikin mummunan halin dabai taba samun kansa a ciki ba. #MAMUH #THE STORY BEGINS #BEST HATE LOVE STORY #BESTROMANCE #AZIZ AY LIMBA #JANNAH ZAD #AYSH....... #CRAZY LOVE #LOVE TRIANGLE ZAFAFA BIYAR KALBIM 500 mamuhgee A DUNIYATA 500 Huguma AJIYA A DUHU 500 Billyn Abdul KIRJIN ME HANKALI 500 Miss xoxo Pay at 0022419171 AccessBank Maryam sani gummi Shedan biya 09033181070 Or mtn vtu at 09032345899*_KALBIM_* _Mamuhgee_ 86 *UMMU_MAHNOOR LUXURIES* (Best luxuries shop) 08034469681 08135142610 Aslm Alaikm ina kuke masu neman luxuries na kayan alfarmar kece raini? Ina masu son su saka sitirar alfarma ta zamani ta manyan mata masu aji da zaa kalleki kallo daya asan sitirar alfarma e kika saka? Shin kunsan me ake nufi sa kayan asalin yan gayu da nuna gayu? Sitirar Alfarma kikeson sakawa? Sitirar da kike ganin manyan mata da ita? Sitirarda zakiyi gayun sallah dake da yaranki a dauka waje kikaje da kanki kika siyota? To kizo ga damarki ta sameki sbd UMMU_MAHNOOR LUXURIES ta kawo miki sauki har gida, Karkice se masu kudi ke iya siya har kema me yar dama zaki samu naki da saukin kudi kuma best quality da kalar zamani data yan gayu, Nidai Mamuh nace duk wadda ke son a buga gayun sallan bana da ita da 'yayanta to tazo gurin UMMU_MAHNOOR LUXURIES tai siyayyar sallanta harma zuwa gaba dan nasan zakuji dadi da fahimtar abinda nake fada akan kayanta💯💯 Abubuwan da zaki samu a gurinta with the best quality na wayayyun mata masu aji yan gayu sune; Atampopi Laces Shadda Materials Shoes Bags Veils Trolleys Jewellerys Oil perfumes Numbers 08034469681 08135142610 Handles Instagram @ummu_mahnoor_luxuries TikTok username @ummu_mahnoor_luxuries Facebook ummu_mahnoor_luxuries ************ FALAQQ" shine abinda bakinsa ya furta da wani sauti me fasa zuciyar datake neman rasa kanta yana yin kanta idaniwansa na sauyawa dukkanin hannuwansa na wata irin rawa. Kafin ya isa ta zube a jikin mama data tareta itama koina jikinta na wata irin rawa sbd jinin daya zubowa daga bakinta wanda ya sakata jin tana rasa kanta itama sbd tinanin zuciyar Falaq din ta riga ta fashe. Yanda ya furta sunanta da karfin gaske gidan ya amsa gabaki daya ya saka dukkanin dan adam dayake gidan tsayawa cak daga inda yake suka jin zuciyoyinsu na tsinkewa. Sayd ne ya fito yana qarasowa palon da tsananin sauri da tsoron idan ba collapsing din da akace kada taiba na karshe ta samu. Tsananin rawan da hannuwansa basu taba yiba hannuwan AZIZ din sukeyi ya ringa goge mata mata bakin da hancin batareda yasan me yakeba yana kiranta bakinsa da hannuwansa suna tsananin rawa jinin na sake fitowa. Mama ma fita hayyacin nata tai tana kokarin riqesa ganin yanda komai nasa yake rawa yana fita hayyacinsa zarewansa na bayyana tuburan yana kiran sunan Falaq din yana jijjigata gabaki daya jikinsa da nata ya lalace da jini. Sayd na shigowa hankali a tsananin tashe wani mummunan burki yaci wanda ya sakasa kusan faduwa yana kallansu zuciyarsa na wata irin tsagawa da karfin gaske. Bude baki yayi da wani irin karfin hali yace "Asibiti,asibiti" Kamar jiran afada AZIZ yake ya miqe da sauri da ita a jikinsa ya nufi kofa Sayd na gaba da tsananin sauri ya fiddo mota hannuwansa na rawa shima, Mama Latif ta cewa maza ya fidda mota ta fito itama da komai nata ke rawa sbd tashin hankali... A jere cikin tsananin tashin hankalin da basu taba shiga ba tin rasa Ummitah suka bar gidan zuwa asibiti babu wanda bai kusan zarewa a cikinsu musamman Ubanta dayake rungume da ita har lokacin yana jin zuciyarsa na mummunan tsagawa. Silalewa ahankali jannah da kafafuwanta suka mutu murus tayi ta zube a tsakiyar palon da aka barta tata zuciyar itama tana kasa daukan dukkanin wannan masifar datake gabanta, Hannuwanta dake rawa ta miqa ahankali ta fara bin takardun dake qasa zube tana karanta sunayen jamaar da suka rasu sbd neman zuciyarta, Wani irin azababben ciwo da radadin gaske kirjinta yakeyi idanuwanta na neman makancewa sbd tsananin radadin hawayen da suke neman sauko musu, Akan takardar datai gefe daban ta fadi ta dora hannunta dayake rawa ta juyota hoton Ummitah da sunanta UMMITAH ABDULAZIZ LIMBA ya bayyana wanda ya sakata fasa wani irin azababben kuka me tsananin ciwo da qunci tana dafe kirjinta setin zuciyarsa tana rintse idanuwanta kukan na tsaga zuciyarta. Masu aiki dake jinta tsit suka sake yi jikinsu na sake tsananin sanyi sbd tausayi. Kuka takeyi sosai kaman zuciyarta zata fashe sbd zallar qunci da rashin madafa, Ciwon rayuwarta takeji, Inama ta jima da barin duniyar, Inama Allah ya bawa familynta a baya sun hakura sun barta tabar duniyar da duka basu samu kansu a wannan kaddarar me nauyi ba, Inama bata rayuwa ba anbar Falaq da mahaifiyarta, Inama ba zuciyar Ummitah ce a kirjinta ba, Inama zaa iya dawo da baya data miqawa Limbas zuciyarsu kowa yayi rayuwarsa yanda ya saba........ Inama zata iya goge wannan mummunan kaddarar akan ahalinta.. Zubewa tayi kwance tana dafe kirjinta cikin tsananin azaba da kukan dayake fitowa daga zuciyarta. Fiddausi ce ta iso ahankali cikin palon ta iso kafafunta a sanyaye kan jannah din tana bin komai dayake gurin da kallo har idanuwanta suka sauka akan fuskan Ummitah itama. Wasu zafafan hawaye ne suka gangaro mata ta juya zata fice sai kuma ta kasa sbd wani irin kuka dayake ratsa zuciyarta da Jannah ke yi a kwance kaman zuciyarta zata mutu. Dawowa tai ahankali tareda durqusawa ahankali ta dafa bayan jannah din tana kasa cewa komai. Jannah bata iya cewa komaiba sai tsananta da kukanta keyi jikinta na rawa ahakali. Ahankali Fiddausi ta bude baki tana kallan fuskan Ummitah dake jikin hoton tace "Ummitah itace duniyar ABDULAZIZ LIMBA gabaki daya, Rashinta shine ya maidasa AZIZ LIMBA wanda babu komai acikinsa sai emptiness, Ya rasa Ummitah falaq ta maye gurbin dayake riqe dashi, Rashin Ummitah ya taba kwakwalwa da hankalinsa da a yanxu rasa Falaq Allah ne kadai yasan kaddarar daya tanadar masa a gaba wadda bama fata sbd AZIZ LIMBA issa pure soul, Naji nasan Kashe Ummitah akai ta hanyar rabata da zuciyarta, Kinsan waye Ummitah a rayuwarsa?? Ahankali idaniwanta na yin ja tafara bayyana mata waye Ummitah da AZIZ LIMBA, Su waye asalin iyayensu hakama waye mama a gurinsu, Waye Sayd a gurin Ummitah da kuma waye asalin mahaifin Falaq tareda yanda rasuwar Ummitan ta sauya rayuwar kowanne a cikinsu musamman AZIZ da irin jinyar dayasha da mutuwar daya kusan yi wanda anan ne ma ya samu duk matsalar da ake tinanin yanada ita.. Dena sauti kukan Jannah yayi sai ahankali kukan ke fita sbd karfinta daya kare tareda zuciyarta da azabar ciwo da radadi, Qunci ne kawai take ji tako ina yana tsagata yana kashe duk wani halittar da Allah yayi a jikinta kalaman Fiddausi na yaga azabtaccen radadi akowane saqo na jikinta da zuciyarta dake karban kowane zancen da ciwonsa dayake yankanta direct. Miqewa Fiddausi tayi ta fita dan kawo mata ruwa ko zata iya dawowa daidai sbd gabaki daya ta koma kalar qunci da tsananin tausayi, Idanuwanta sunyi munin da ko gani sosai bata yi dasu. Awanni ta share a zube tsakiyar palon tana kukan da har zuciyarta ta kasa dauka kafin ahankali ta tashi hannuwanta babu karfi ta tattara takardun palon ta fice dasu. Fitowa tayi babu karfi ko kadan a jikinta bare zuciyarta ta fice daga gidan. Yau securities basu hanatava sbd ganin yanayinta kamar ta zare dan ko gani sosai batayi gashi kuma dai suna cikin tsananin jimamin abinda yake faruwa dan haka babu me energy na hayaniya. Tafiya takeyi da kafa tana dafe zuciyarta dakejin kaman zata buga, Ciwon gaske take mata ba iya na qunci ba ciwon azaba take mata. Tafiya tayi sosai kafin ta samu motar data tsayar ta shiga tana rintse idanuwanta da babu kyan gani ko kadan tanajin tsananin tausayin AZIZ LIMBA da ahalinta da rayuwar kowannensu ta lalace a daidai gabar da ake yanzu dukkaninsu sbd ita, Kaddara ta riga ta hada rayuka biyi a guri daya, Gangar jikin Zaadens da Zuciyar Limbas wanda kowannesu a yanzu neman mafitar fita daga wannan mummunan kaddadar suke. Asibiti ta iso Allah yasa Saleem yana dawowa kenan shima dan haka shine ya biya mai motan yana kallanta cikin mummunan tsoron wata masifar ce ta kunno kenan. Ciki sukayo tana handa hanya bata gani sosai hakama jikinta yayi weak sosai.... Suna isa dakin da Dad yake zaune Maheer yana basa tea ahankali yana sha Mimi ma na zaune gefe tayi shiru tareda nisa a tinani sosai batama san tinanin datake ba sbd depression da yayi mata mummunan kamu itama. Shigowan Jannah din da yanayinta ya sakasu duka juyowa kanta suna kallanta da mamakin ganin yanda ta koma kamar mahauciyar da batada gata ko kadan. Takardun hannuwanta ta dago hawaye masu tsananin ciwo suna gangarowa daga cikin idaniwanta ta miqawa Maheer tana bude bakinta dayayi tsananin nauyi muryanta bata fita sosai tace "Shin dukkanin abinda yake cikin nan da gaske ne? Shin ni har nakai matsayin macen da zaa hallaka rayuka da dama sbd na rayu? Shin mummunan kaddarata takai na saka imanin ahalins ko nace iyayena fita su iya kisan mutane da dama harda me tsohon cikin datake rokon a saukaka mata????? Zubewa tai qasa tana fasa sabon kukan dayake fitowa rin daga zuciyarta tana rintse idanuwanta hawaye na fita sosai. Dad kasa dago idaniwansa da sukai jajir yayi yana jin ciwo da radadin da Jannah din ke ji na samunsu da wannan mummunan aikin da shine yake lalata rayuwar kowa a yanzu harda tata din da sukai komai dan ta inganta. Maheer kuwa damqe file din yayi shima ciwo da radadin abin na saka idaniwansa jajir hannuwansa na rawa sautin kukanta na ratsa kowa dakin. Mimi ce ta kalli Dad gabanta na faduwa kafin ahankali ta dawo da kallanta kan Maheer da hawaye masu tsananin ciwo suka gangaro masa... Jin tayi gabanta ya sake mummunan faduwa ta kalli saleem da shima mafi girman tashin hankalin ya shiga yana kallansu kafin ya miqa hannunsa yana rawa ya ciro file din daga hannun Maheer ya fara budewa yana karanta abubuwan dake a ciki a fili muryansa na wani rawar tashin hankali da firgici.... Yana isowa na Ummitah ya ambaci sunanta wanda yake hade dana AZIZ LIMBA take Mimi tayi baya tana jan numfashi ta fada jikin bango shima Saleem dagowa yayi hawyae na bin fuskansa ya kalli jannah wadda ta bude baki tace "Zuciyar Ummitah Limba ce a kirjina, Zuciyar mahaifiyar Falaq ce take bugawa a kirjina, Zuciyar macen da aka kashe ce da tsohon ciki ce a kirjina, Zuciyar macen da a nata ahalin itace haske kuma idaniya a kirjina......... Maheer ne yayi saurin miqewa yana isa ga jannah din cikin dana sani da ciwo Yace "Duka sbd ki rayu ne Jannah" Wani mummunan jan numfashi Mimi tayi tana zubewa qasa sbd tsananin shock da tashin hankalin jin abinda bata taba jiba.... Saleem da ganinsa da jinsa ya dauke take shima zubewar yayi qasa zaune yana qurawa Maheer da Dad idaniwansa... Ahankali Maheer ya bude baki yafara fadar duk abubuwan da suka aikata din wanda take zuciyar Mimi da Saleem harma da jannah suka kasa dauka Mimi tafara jan Numfashinta dake neman katsewa tamkar me asthma, Ganin tana neman rasa numfashinta Saleem da baya gani sosai yayi kanta sa rarrafe yana kokarin ambatar sunanta amma bakinsa ya kasa buduwa hakama hannuwansa shima sun mutu sai yaji kawai komai baya motsawa a jikinsa hawaye suka fara gangaro masa kafin yayi yunquri yana ji yana gani Mimin ta juye a gurin numfashinta ma dakatawa cak. Ita kanta jannah a jikin Maheer ta zube dan haka dole Maheer din hankali tashe ya nemo likitoci aka kwashesu su ukun zuwa emergency. Dad da maheer kuwa jigum sukai babu me iya cewa komai suka zubawa sarautar Allah ido suna fatan ba wannan shine karshensu ba na shedar da mutuwar rayuka mafi soyuwa a rayuwarsa akan laifin da sune suka aikataba. Har dare babu labarin komai da kowa a tsakanin su ukun dan haka Dad da Maheer din suka sake shiga mummunan yanayi na dana sani da damuwa me tsanani. #MAMUH #BEST LOVE #AZIZ AY LIMBA #JANNAH ZAD #LIFE CHANGING #NEW LIFE #NEW BEGINNING #AYSH ZAFAFA BIYAR KALBIM 500 mamuhgee A DUNIYATA 500 Huguma AJIYA A DUHU 500 Billyn Abdul KIRJIN ME HANKALI 500 Miss xoxo Pay at 0022419171 AccessBank Maryam sani gummi Shedan biya 09033181070 Or mtn vtu at 09032345899*_KALBIM_* _Mamuhgee_ 87 *UMMU_MAHNOOR LUXURIES* (Best luxuries shop) 08034469681 08135142610 Aslm Alaikm ina kuke masu neman luxuries na kayan alfarmar kece raini? Ina masu son su saka sitirar alfarma ta zamani ta manyan mata masu aji da zaa kalleki kallo daya asan sitirar alfarma e kika saka? Shin kunsan me ake nufi sa kayan asalin yan gayu da nuna gayu? Sitirar Alfarma kikeson sakawa? Sitirar da kike ganin manyan mata da ita? Sitirarda zakiyi gayun sallah dake da yaranki a dauka waje kikaje da kanki kika siyota? To kizo ga damarki ta sameki sbd UMMU_MAHNOOR LUXURIES ta kawo miki sauki har gida, Karkice se masu kudi ke iya siya har kema me yar dama zaki samu naki da saukin kudi kuma best quality da kalar zamani data yan gayu, Nidai Mamuh nace duk wadda ke son a buga gayun sallan bana da ita da 'yayanta to tazo gurin UMMU_MAHNOOR LUXURIES tai siyayyar sallanta harma zuwa gaba dan nasan zakuji dadi da fahimtar abinda nake fada akan kayanta💯💯 Abubuwan da zaki samu a gurinta with the best quality na wayayyun mata masu aji yan gayu sune; Atampopi Laces Shadda Materials Shoes Bags Veils Trolleys Jewellerys Oil perfumes Numbers 08034469681 08135142610 Handles Instagram @ummu_mahnoor_luxuries TikTok username @ummu_mahnoor_luxuries Facebook ummu_mahnoor_luxuries *************** Cikin dare sosai Likitoci suka samu fitowa daga dakin Falaq zuciyoyinsu da fuskokinsu babu farin ciki ko kadan saima tausayinta dana familyn nata da suke asibitin a cikin mummunan yanayi na sanyi. Dr Ashir ne ya tsaya gabansu tareda sauke ajiyar zuciya me sanyi yana kallan AZIZ LIMBA wanda idanuwansa sukai ciki gabaki daya sbd tsananin tsoro da damuwar data gama cinye dukkanin kuzari da jarumta tareda karfin halinsa. Irin kallan da dr Ashir yake masa ya saka dukkaninsu juyawa suna kallan AZIZ din wanda ya koma ahankali ya zauna yana dauke idanuwansa daga kan ashir din Mama tai saurin dafasa tana riqe hannunsa cikin kokarin basa kariya da kwarin gwiwan da itama bata dashi. "Ta riga takai stage din datake buqatan heart transplant batareda bata lokaci ba ko daukan lokaci ba...." Ahankali ya zame daga kujeran dayake zuwa qasa yana qanqame hannun mama datake riqe dashi ya cusa fuskansa a tafin hannuwanta wasu hawaye masu tsananin zafi da tashin hankali suna gangaro masa jikinsa na daukan rawa gabaki daya wanda ya saka kowa dayake gurin tsit kafin kukan daya kasa riqewa ya kubce masa sbd kaman ana fada masa ne Falaq tafiya zatai ta barsa kenan.. Sautin kukansa ne ya tayarda tsikar jikin dukkanin wanda yake gurin yana ratsa zuciyoyinsu, Jijjiga jikinsa keyi sosai fuskansa na tafin hannuwan mama datake hawayen tausayinsa har cikin ranta, Sayd ma silalewa yayi ya zauna a qasa hawaye masu tsananin zafi da radadi na tsinke masa sbd kai tsaye kaman dama ce aka sanar dasu ta kwanakin dasuka ragewa Falaq a duniya. Mama ma ganin kukan Sayd sai ta kasa riqe sautin kukanta ta rintse idanuwanta tana sake jin saukan hawayen AZIZ masu zafi a tafin hannunta. Dr Ashir da suke saka hawaye taruwa a idanuwansa barin gurin yayi yana jin tausayin familyn gabaki daya sbd shi kansa yasan samun donor abu ne me wuyar gaske da ahaka suna ji suna gani lokacinta zaiyi tabar duniya. Daqyar mama ta iya kama hannunsa ta dagar dashi ta kama hannun Sayd shima dayake kuka rasa 'yarsa da har yau batasan matsayinsa na mahaifintaba, 'Yar dayake kallo a lokutan quncinsa ya samu sassauci da sanyi, 'Yar dayake wa kallan mahaifiyarta daya rasa, 'Yar da har yau bata taba kallansa a uba ba bare ambatarsa da sunan uba ko so daya ba... Dakin falaq din mama ta shiga dasu ta isa dasu har bakin gadonta ta saki hannuwansu suna kallan yanda Allah ya Maidata a lokaci daya ba kyan gani, Oxygen ne da wasu abubuwan a fuskanta da bakinta harma da kirjinta, Tayi haske a lokaci daya tai wani irin jemewa idanuwanta a rufe, Kallo daya zakai mata kasan ciwo me girma ne a tattare da ita wanda Allah ne kadai yasan ko zata tashi kokuwa tafiyarta zatai itama ta huta da wannan duniyar me wahalar zama. Silalewa AZIZ yayi ya zauna a gefe yana kallanta sbd yanayinta dake nuni da azababben ciwone take cikinsa duk da bata hayyacinta.. Sayd ma sunkuyar da kansa yayi yana zuba mata dukkanin idanuwansa jikinsa a mace. Shiru dakin yayi babu me motsi, Ayau falaq datake da gatan da dayawa basada gata a kwance numfashin datake shaqa ma na Oxygen ne zuciyar da zata rayu take buqata, Kudi da gatanta ba zasu iya bata hakan ba, Soyayyar mahaifinta bazata iya bata hakan ba sai abinda Allah yaga damar yi da ita. Tsawon Lokaci ahakan har aka fara kiran asuba suka fito AZIZ na gaba Sayd na gefensa kowannensu idanuwansu sunyi nauyi sosai. Masallaci suka nufa sukai sallah suka zauna suna adhkar har gari yai haske kafin AZIZ ya dago idanuwansa ya kalli Sayd tsawon seconds kafin ya bude baki Ahankali ya furta "Ka sanar da Dr Nico komai da ake ciki a sakamu na list din gaggawar neman donor" Gyada kai Sayd yayi yana sauke numfashi. A kusan qasashe 6 Sayd ya buga da neman zuciyar cikin lokacin daya ragewa Falaq din wadda take qara wani irin sauyawa daga kwancen tana rasa duka albarkar jikinta. Duk yanda suke tinanin zasu iya riqe abin sun kasa su kansu a cikin budadden qunci suke daya nauyaya zuciyoyinsu. Gida suka dawo aka baro Fiddausi dataje can, Tsit gidan yayi ga dining an jere abinci amma babu wanda ya iya fitowa a cikinsu kowa na daki. Wanka yayi ya sauya kaya ya zauna yana buga wayoyi a wayarsa kansa na zarewa ahankali ahankali gurin neman ta inda zai samu zuciyar dasawa 'yarsa. Acan asibitin Zaadens kuwa Saleem ne ya fara dawowa daidai kafin jannah wadda ta zubawa mahaifinta dake zaune gabanta idanuwanta da sukai tsananin laushi. Mahaifinta kaunarsa a jininta take da duk laifin da zai aikata a duniyarnan bazata taba dena so da kaunarsa ba, Bazata taba gudunsa ko qyamarsa ba,bazata taba jin tsanarsaba, Kaunarsa ce take sake rufesa da tausayinsa sbd duka wannan mummunan lamarin daya faru ya farune sbd kaunarta da shedan daya shiga zuciyarsu ya gurbata tawakkalinsu. Ahankali wasu hawayen baqin ciki da dana sani tareda kunyar yarsa suka gangarowa Dad ya dago ya kalleta itama shi din take kalla idanuwanta na tsiyayar hawaye. Saukar hawayensa Kan tafin hannunsa dayake bude ne ya sakata rintse idanuwanta da karfi tana jin zuciyarta na tsananta ciwon ganinsa ahakan... Bude bakinsa yayi Ahankali cikin sanyi yace "Akwai son zuciya da rinjayar shedan a lamarin da muka aikata, Nayi dana sanin nema miki zuciyar datake jirjinki bata hanya halastacciyaba sbd kema kin shiga matsalar da mune muka janyota, Jannah ni mahaifi ne da idanuwana sika rufe akan kaunar danakewa 'yata a baya, Kuma a yanzu ma na shirya zama uba da idanuwansa zasu rufe akan kaunar dayakewa 'yarsa na aminta na shirya karban da fuskantar sharia sbd hana rayuwarki shiga quncin da babu fita, Bakida masaniya dan haka zan miqa kaina da kaina sbd na kasa baki farin ciki daga karshe sai kuka da qunci...... Wani irin kuka me tsima zuciya ta fasa tana fadawa jikinsa ta rungumesa da karfi tana girgiza kai quncinta da radadin zuciyanta na tsananta. Rungumeta yayi shima yanajin kasawarsa da lalata rayuwar duka 'yayansa a matsayinsa na uba. Maheer dake gefensu kuka yakeyi sosai shima har yana jijjiga zuciyarsa na radadi shima yana jin zai iya bin mahaifinsa a duk matakin da zai dauka a wannan rayuwar me kyau da mara kyau dan haka idan mahaifinsa ya aminta dasu miqa kansu su karbi hukuncin daya kamata ya aminta da hakan ya shirya binsa har lokacinda da zaa kashesu kaman yanda suka kashe. Kuka sukeyi gabaki dayansu a dakin cikeda tsananin so da kaunar junansu da haryanzu babu abinda ya sauya daga cikinta, Saleem ma mahaifiyarsa da likita ya sanar dashi ta samu paralys ya rungume yana wani irin kuka mai tsima zuciya. Jannah dagowa tayi ta kalli mahaifinta kafin ta maida kallanta kan Maheer dayake gefenta riqe da hannunta daya ta bude baki cikin sanyi tace "Neman tuba da yafiya a gurin Allah shine farko kafin komai, Insha Allah zamu cinye wannan jarabar Dad" Dakin Mimi suka nufa dukkaninsu idanuwa a jeme a can suka tararda mugun labarin daya qarasa collapsing duniyarsu gabaki dayanta. Sabon zama suka dora na jimami har dare. Tsakar dare Mimi ta farka ta bude idanuwanta ahankali daqyar cikin wani irin sanyi tanajin dukkanin quncin zuciyarta ya yaye ganin ahalin dai daga karshe kansu ya sake hadewa basu rabu ba duk da munin aikin dasu Dad suka aikata. Akan Saleem ta tsayar da idanuwansa tai masa kallan mintina ya saka hannunsa cikin nata yana hango kewan Ammar a cikeda idaniwanta wanda babu bakin furtawa, Maida idanuwanta akan Maheer tayi tana jin tsananin tausayin kaddarar data hau kansu wadda batasan hukuncin da zasu fuskanta ba amma koma menene tana masa fatar samun sassauci da rayuwa me kyau a gaba idan yanada rabon tsallakewa. Maida idaniwanta tai kan jannah da itama ita take kallo idaniwanta sun bushe sunyi jajir babu abinda yake cikinsu sai qunci da damuwa. Hawayene suka gangaro daga gefen idanuwan Mimin tana jin tausayin rayuwar jannah da batasan yaya zata kasance ba idan ta wayi gari batareda gata da dukkanin ahalinta... Maida kallanta kan Dad tai wanda kallo daya tai masa idanuwanta suka rufe ahankali. Maheer ne yafara kiran sunanta ahankali yana miqewe tsaya zuwa ga fuskanta yana tabawa hannuwansa na rawa. Saleem ne ya fahimci Mimi ta riga tabar duniyar ta barsu rai yayi halinsa. Maheer kasa yadda yayi da hakan ya fara jijjigata yana kiran sunanta. Jannah ma fadawa tai kan Mimin tana kiran sunanta cikin wani matsanancin halin daya cinye karfi da zuciyarta. Dad sunkuyar da kai yayi hawaye na tsiyayo masa daga karshe dai duka sunata girban abinda suka aikata ta hanya me ciwon dayafi wanda suka saka mutane, Ahankali Allah ke dandana musu zafi,ciwo da radadin rashi wanda suka take suka saka mutane da yawa a ciki. Tsit asibitin tai sbd kukan Jannah da Maheer dayake tashi a dakin yana fitowa waje ahankali... Saleem suman zaune yayi har lokacin hannunsa na cikin na mahaifiyarsa yana jin zuciyarsa na mutuwa daga komai na duniyar gabaki daya. A cikin daren suka dawo gida da gawar mimi wanda zaayiwa janazah da safe. Kwanan zaune sukai dukkaninsu a palo Sunyi kuka har hawayen kowannensu sun qafe babu komai sai jajayen idanuwa. Washe gari karfe goma na safe akai janazah din Haj Mimi Zad wadda ta samu mutane ba laifi ciki hadda Baba alhassan da alh Saad sbd a limbas babu me kwanciyar hankali ko tinanin da zai iya zuwa. A lokacinda aka dawo tinda ba zaman gaisuwa zaayiba tini kowa ya watse aka bar jannah kadai da masu aiki shiru gidan babu kowa ba komai sai tarin damuwa da qunci. #MAMUH ZAFAFA BIYAR KALBIM 500 mamuhgee A DUNIYATA 500 Huguma AJIYA A DUHU 500 Billyn Abdul KIRJIN ME HANKALI 500 Miss xoxo Pay at 0022419171 AccessBank Maryam sani gummi Shedan biya 09033181070 Or mtn vtu at 09032345899*_KALBIM_* _Mamuhgee_ 88 *UMMU_MAHNOOR LUXURIES* (Best luxuries shop) 08034469681 08135142610 Aslm Alaikm ina kuke masu neman luxuries na kayan alfarmar kece raini? Ina masu son su saka sitirar alfarma ta zamani ta manyan mata masu aji da zaa kalleki kallo daya asan sitirar alfarma e kika saka? Shin kunsan me ake nufi sa kayan asalin yan gayu da nuna gayu? Sitirar Alfarma kikeson sakawa? Sitirar da kike ganin manyan mata da ita? Sitirarda zakiyi gayun sallah dake da yaranki a dauka waje kikaje da kanki kika siyota? To kizo ga damarki ta sameki sbd UMMU_MAHNOOR LUXURIES ta kawo miki sauki har gida, Karkice se masu kudi ke iya siya har kema me yar dama zaki samu naki da saukin kudi kuma best quality da kalar zamani data yan gayu, Nidai Mamuh nace duk wadda ke son a buga gayun sallan bana da ita da 'yayanta to tazo gurin UMMU_MAHNOOR LUXURIES tai siyayyar sallanta harma zuwa gaba dan nasan zakuji dadi da fahimtar abinda nake fada akan kayanta💯💯 Abubuwan da zaki samu a gurinta with the best quality na wayayyun mata masu aji yan gayu sune; Atampopi Laces Shadda Materials Shoes Bags Veils Trolleys Jewellerys Oil perfumes Numbers 08034469681 08135142610 Handles Instagram @ummu_mahnoor_luxuries TikTok username @ummu_mahnoor_luxuries Facebook ummu_mahnoor_luxuries ************** Kwana biyu shiru rayuwa ta sauya a zadeens babu me fita babu me zuwa, Walwala da farin ciki ya zama tarihi a rayuwarsu ko abinci ba koyaushe suke fitowa ci ba... A wannan halin ne suka wayi gari Saleem yabar komai nasa ya bar gida baa gansaba. Da farko sun jira ne har dare tukuna. Har karfe 12 na dare Saleem bai dawoba hakama wayoyinsa ya barsu gida dan haka hankalinsu ya fara tashi. Maheer ne ya fita a cikin daren yafara nemansa cikeda damuwa. Suma su jannah da dad hankalinsu tashi yake sake yi dan haka suka ringa kiransa suna son jin ko ya gansa din. Yawon garari Maheer ya ringa yi cikin daren har asuba baiga Saleem ba dan haka ya dawo gida. Wuni daya ba saleem ba labarin, Wuni biyu dan haka suka tabbatarda ya tafiyarsa ne sbd bazai iya rayuwa a cikinsu b Mimi ba Ammar ba. Damuwar Dad ninkuwa tayi dan haka Maheer ya sake tada musu shirinsu na barin qasar su koma inda zasu bude sabuwar rayuwa. Jannah da passport dinta baya tareda ita dole shiryawa tayi ta tafi Limbas dauko Kayanta masu mahimmanci su passport da id cards dinta. Se dare ta isa gidan sbd batason Falaq ta ganta ko ita taga falaq kunyarta da ciwon ganinta takeyi, Kunyar kallanta da zuciyar Ummitah a kirjinta takeyi, Kunyar kallan mama da zuciyar 'yarta a kirjinta takeyi dan hakanne take sake jin nutsuwa da rabuwa dasu rabuwa ta har abada. Karfe 10 na dare ta isa da motarta tai parking motar a can waje bata shigo da ita ba sbd batasan ma asan tazo har ta tafi. Securities gate suka bude mata ta shigo kai tsaye ta nufi ciki. Main Living room ko data shigo babu kowa tsit gidan hakama duhu ankashe wutar koina. Kai tsaye dakinta ta nufa kafafunta a sanyaye ta bude ta shiga ahankali ta isa bakin gadonta ta zauna a darare idanuwanta na zafin quncin dayake kirjinta. Hoton falaq dayake aje gefen hotinan familynta dake gefen beside ta zubawa ido tana kalla tanajin tsananin kauna me karfin gaske datakewa falaq tana taso mata tana danne kirjinta, Hawaye ne masu tsananin zafi sika silalo mata ahankali tana daukan hoton ta rungume hawayenta na qara gudu sbd tinawa da ranar da Falaq din tafarajin Zuciyar mahaifiyar data haifeta aka cire aka saka mata irin shock din data shiga wanda batasan yaya ta iya handling da karban komai ba haryaxu' A wane hali zuciyarta take akan zancen yanzu? Ta tabbatarda Falaq ta tsaneta ne shiyasa bata taba nemanta ba ko a lokacinda ta rasa mahaifiyarta tana tsananin neman wani a tareda ita. Miqewa tayi da Hoton a jikinta ta nufi inda passport dinta da id cards dinta suke su kadai ta dauka ta nufo kofa hawayen fuskanta na tsananta gudun radadin datake ji a zuciyarta na rabuwa da falaq da wanda zuciyarta ke tsananin yiwa son dayake kaddara da dana sani garesa. Fitowa tayi daga dakin kukanta na tsananta, Taku biyu tayi tayi karo da mutum a gabanta tsaye cak. Babu haske sosai sai kadan wanda na dakinta da bata rufe bane yake haskosu. Kayan hannunta ne suka zube qasa sbd yanda ta bugu dashi batasan dashiba, Qin dagowa tayi sbd qamshinsa daya tabbatar mata da wanda ta sani dinne.... Shima qin kallanta yayi ya xubawa passport dinta daya fadi qasa da id cards dinta idaniwansa da sukai tsananin nauyi da ja sbd mummunan halin dayake ciki na yarsa dayake ji yana gani yana neman rasawa. Shiru sukai babu wanda ya motsa bare kallan dan uwansa sai idaniwansa dake kan passport dinta har lokacin zuciyarsa na sosuwa me tsananin ciwo da zafi tarewa yankewa..... Durqusawa tayi ahankali ta miqa hannunta zata dauka ta wuce sbd zuciyarta dake neman dena bugawa a gabansa din. "Kin zabi guduwa dasune sbd tseratar dasu bayan girman cutatarwa da quncin da suka saka mutane da dama hadda falaq da batasan komai da kowaba?? Zuciyar Ummitah bazata taba zabar wainda suka cutatar da AZIZ da falaq ba, Ashe a jininku yake kenan ba a zuciya bane...... Rintse idanuwanta tai maganganunsa na sukar kirjinta hawaye masu zafi suka gangaro mata ta bude baki tareda dagowa ta kallesa ta bude baki cikin jin ciwon kalamanta ita kanta tace "Zuciyar Ummitah ce a kirjinta amma jinin mahaifina ne yake yawo a jikina yana harbawa har cikin zuciyar Ummitan datake kirjina, Zuciyar Ummitah sonka takeyi tana kaunar Falaq amma kuma jinin Zaadens ne yake yawo a jikina bamu taba juyawa namu baya ba komai tsanani, girman son da zuciyar Ummitah takewa AZIZ LIMBA bazai taba wanke kaunar mahaifin datake jinin gangar jikin da zuciyar ummitan takeba, AZIZ LIMBA Zuciyata na maka tsananin son da bazan iya cirewava har abada sbd zuciyar datake kirjina wannan shine kaddarata danake son gogewa kaina" Cikin idaniwansa dayake kallanta da wani irin radadi tayi tana tsiyayo hawayen dake bayyanar da tsananin sonsa dayake kasheta kowace daqiqa. Kuka ta fashe dashi mara sauti tana rintse idaniwanta ta zube qasa tana dukan kirjinta da karfi tana kukan dayake qarasa yamutsar da kansa yana neman qarasa zarewa shima..... Juyawa yayi zai bai gurin ta bude baki cikin wani irin qunci da kuka tace "Dan Allah ka rabani da Zuciyar nan daga kirjina, Dan Allah ku rabani da ita nima na gaji, Na gaji banaso, Inaso na kwanta na huta kamar Ummitah, Bazan iyaba,ciwo nake ji, Zuciyata bazata iya daukaba, Bazan iyaba inason hutawa nima, Inason hutawa kaman Ummitah da Mimi........ Wani irin kukan daya saka qafafunsa sarewa ya zube qasa shima takeyi tana maganar wadda takeyi cikin tsananin qunci da ciwo da radadin dayake cikeda rayuwarta da babu abinda ya rage sai baqin ciki da damuwa. Shi kansa hutawan yakeson yi kaman Ummitah da mahaifinsa da mahaifiyarsa, Baida abinda ya rage masa a duniya sai Falaq wadda itama zata tafi tabarsa, A yanxu tabbas so yake ya bar komai ya tafi ga iyayensa da Ummitah sbd bazai iya daukaba... Miqewa tayi kukanta na qaruwa ahankali mara sauti tana neman barin gurin jikinta na rawa ta taka kafarsa ta sake zubewa qasa akansa. Tafin hannuwanta biyu ne suka sauka akan fuskansa da hawaye ke gangarowa ahankali. Jin hawayensa a tafin hannunta ya sakasa zubowa da wasu hawayen..... Hannuwana biyu ya saka akan nata ya rufe fuskansa dasu yana girgiza mata kai wani irin kuka mara sauti yana fito masa.... Itama kukan takeyi tana girgiza masa kai alaman rabuwansu shine mafi alkhairi..... Yanda yake kukan ne ya saka kukanta qaruwa sosai ta qanqame fuskansa tana kukan datake neman wanda zataiwa tsawon lokaci dan haka dukkanin quncin dayake dunqule a kirjinta kukansa takeyi tana zubewa a jikinsa ya qanqameta tareda hade goshinsu guri daya hancinsu na gogar na juna. Ahankali muryansa na rawa ba sauti a galabaice yace "Pls dont" Girgiza kai tayi kukanta na qaruwa ta bude baki tace "I cant" Sake bude baki tayi zata sake cewa i cant ya hade bakinsa da nata yana hanata fada kukansu na qaruwa duka su biyun sbd abinda bata saniba a gobe ne da safe zaa kama iyayenta sbd anriga an gama binciken komai a goben kamasu zaayi a hanya mafi muni. Girgiza kai tayi hawayenta na sake gudu sosai bakinsa na cikin nata cikin kukan suke kissing juna ahankali yana sake qanqameta itama rungume kansa tayi tana jin inama bata wannan kaddarar suka hadu ba, Inama haduwa sukai suka kamu da son juna kaman hakan suyi aure kaman kowa familynsu na son juna da girmama juna, Inama itace uwa shikuma uban falaq suke suka haifeta ta hanyar soyayya me dadi da kwanciyar hankali dika babu wannan. Kissing juna sukeyi ahankali yana jin zuciyarsa zata buga da abinda yake ji a cikinta gameda ita din.... Ita kanta tasani soyayyarsa masifar da zata iya hallaka ce dan haka ta bude idanuwanta da sukai jajir da kuka suka kumbura sosai ta sauke a fuskansa hawayenta na tsananta gudu shima ita din yake kallo duniyarsa na juyawa yana jin kirjinsa na sake nauyi me karfin gaske akanta. Ahankali ya fara zare mata rigar jikinta yana dora bakinsa kan nata yana kissing dinta cikin tsananin sanyi da son maidata macen Limba daga yau..... Ita kanta zuciyarta ta riga ta amintar mata da zama daya dashi a daren da zasu rabu kuma bazata taba regretting ba dan haka ahankali ta rufe idanuwanta tanaji yana kokarin rabata da Rigar jikinta..... wayarsa data fado ce daga jikinsa tayi haske sunan Sayd tsaf ya bayyana akan kiran daya shigo wayar..... Cak ya dakata daga abinda yakeyi yana kallan fuskanta datake hawaye har lokacin sbd zuciyarsu su dukan ta dade da mutuwa akan juna..... Wayar ya miqa hannu a sanyaye ya dauka tareda saka handsfree sbd bazai iya dagawaba dan zuwa lokacin ciwon kirjinsa ya gama gauraye jikinsa. "Falaq ta farfado sedai aman jinin ya dawo, Hamma muna rasa Falaq......" cikin wani irin kukan daya saka zuciyar AZIZ dena bugawa Sayd ya fada maganar... Ita kanta jannah mummunan bugawa zuciyarta tayi ta kallesa sedai kokarin kamuwa da attact yakeyi wanda ya sakata ambatar sunansa da karfi wanda hakan ya fiddo da mama daga daki da sauri wadda batada lafiya sosai ma daurewa kawai takeyi. Su Fiddausi ma duka fitowa sukai ana kunna wutar palon haske ya bayyana... Yanayin da suka ga AZIZ ne ya hana mamakin ganin jannah kwata kwata sbd attack din gaske ya samu a take. Securities aka kira cikin matsanancin tashin hankali aka fiddo dashi zuwa asibiti cikin sabon tashin hankalin daya samesu. Koda suka isa asibiti cikin gaggawa aka karbesa sai alokacin jannah ta isa dakin falaq zuciyarta na wata irin mummunan bugawa. Tana tura dakin tin a kofa ta zube qasa zaune tana rintse idanuwanta cikin hawaye kukan na kasa zuwama sbd gabaki daya karfinta da rayuwarta da suka qare yanzu agun kuka. Sayd ne a dakin dukkanin Alamun tafiya da nisan ciwo ya gama bayyana a tattareda Falaq din dan haka ayau yayi kukan da ko lokacin mutuwar Ummitah baiyiba sbd a yanzu duk mai imani ya kalli Falaq a yanda ta koma imaninsa zai qaru. Kukan da jannah keyi tin tanada karfi har karfinta ya qare a dakin ta kwana zaune. Karfe goma na safe Falaq ta sake bude idaniwanta ahankali akan fuskan jannah dake jeme gabanta gabaki daya ta koma kamar ba jannah zad ba ta jeme ta bushe sbd masifar dasuke ciki. Ahankali ta motsa hannunta daqyar cikin sanyi ta dora akan na jannah dake gefen nata hawaye masu radadi suna gangaro mata na tsananin kaunar jannah din da tausayin Daddynta dazai shiga wani halin rashinta kaman yanda ya rasa mahaifiyarta. Ahankali jannah ta dago ta zubawa falaq ido idanuwanta na bushewa da radadi jajir ba hawaye. Kasa magana dukkaninsu sukai har aka bude kofar dakin AZIZ daya koma kalar tausayi shima aka turo a kujera idaniwansa akan falaq wadda ta maida idaniwanta akansa hawaye naci gaba da gangarowa daga idaniwanta. #MAMUH ZAFAFA BIYAR KALBIM 500 mamuhgee A DUNIYATA 500 Huguma AJIYA A DUHU 500 Billyn Abdul KIRJIN ME HANKALI 500 Miss xoxo Pay at 0022419171 AccessBank Maryam sani gummi Shedan biya 09033181070 Or mtn vtu at 09032345899*_KALBIM_* _Mamuhgee_ 89 *UMMU_MAHNOOR LUXURIES* (Best luxuries shop) 08034469681 08135142610 Aslm Alaikm ina kuke masu neman luxuries na kayan alfarmar kece raini? Ina masu son su saka sitirar alfarma ta zamani ta manyan mata masu aji da zaa kalleki kallo daya asan sitirar alfarma e kika saka? Shin kunsan me ake nufi sa kayan asalin yan gayu da nuna gayu? Sitirar Alfarma kikeson sakawa? Sitirar da kike ganin manyan mata da ita? Sitirarda zakiyi gayun sallah dake da yaranki a dauka waje kikaje da kanki kika siyota? To kizo ga damarki ta sameki sbd UMMU_MAHNOOR LUXURIES ta kawo miki sauki har gida, Karkice se masu kudi ke iya siya har kema me yar dama zaki samu naki da saukin kudi kuma best quality da kalar zamani data yan gayu, Nidai Mamuh nace duk wadda ke son a buga gayun sallan bana da ita da 'yayanta to tazo gurin UMMU_MAHNOOR LUXURIES tai siyayyar sallanta harma zuwa gaba dan nasan zakuji dadi da fahimtar abinda nake fada akan kayanta💯💯 Abubuwan da zaki samu a gurinta with the best quality na wayayyun mata masu aji yan gayu sune; Atampopi Laces Shadda Materials Shoes Bags Veils Trolleys Jewellerys Oil perfumes Numbers 08034469681 08135142610 Handles Instagram @ummu_mahnoor_luxuries TikTok username @ummu_mahnoor_luxuries Facebook ummu_mahnoor_luxuries Miqewa jannah tayi ta fice daga dakin tabar asibitin ma gabaki daya tana zuwa gida. Tin daga nesa taga gurin a tsananin cike sosai da sauri ta qaraso tana ratsa mutane harta isa gate din gidan wanda yan media da jamian tsaro sukaiwa mummunan kawanya aka fito da Dad dinta daure da cuffs wani irin mugun daurin daya sakata tahowa da gudu kansa Maheer na bayansa shima a daure idaniwansu jajir. Da gudu tayi kansu tana fasa wani irin kukan dayake neman fasa zuciyarta tana kiran sunasu. Kallanta Dad yayi idaniwansa cikeda wani irin ciwo me radadi yace "Jannah kiyi hakuri na kasa zamowa gatanki a lokacin da bakida kowa kike buqatanmu" Girgiza kai takeyi tana kuka me tsanani tana jin kamar ranta zai bar jikinta. A mota aka sakasu aka tafi dasu anata musu hoto mutane wasu harda jifansu. Ana barin gurin dasu zubewa tayi a gurin qasa tana wani irin kuka me tsanani da tsima rai. Miqewa tayi kamar zararra tayi cikin gidan taje dauko file dinta ta fito ko gani batayi ta hau mota tayi asibiti tana isa gaban AZIZ ta tsaya tana masa wani irin kallon dayake cikeda wata irin tsanar gaske. File din hannunta ta daga ta kunnawa wuta ta jefar a gabansa ta dago ta kallesa hawayen idaniwanta na gangarowa tace "Ayau inason Ka cire zuciyar kirjina ka bawa falaq zuciyar mahaifiyarta sbd ayau ni Jannah Zad banason bana kaunar duk wani abu dayake na Limbas, Ayau ni jannah zad na zabi barin duniya na baka abinda shine ya hadani dakai, Idan zuciyar Ummitah zata cire maka fushi da fansar datake cikeda ranka ayau na baka damar ka cire banaso na gaji, Na gaji, Na gaji, Inason hutawa.... Zubewa qasa tai tana kukan daya saka dukkanin su mama dake gurin yin tsit banda Falaq datake kukan itama tanajin indai sai raba jannah da zuciyar dake kirjinta ita kam ta hakura da rayuwa.. AZIZ file din data kona a gabansa wanda shine zai bawa tasa yar samun sabuwar rayuwa a duniya sbd a cikine manyan bayanan da zasu saka a iya bawa falaq zuciyar daya daga cikinsu suke, A ciki manyan original bayanan da zasu saka a wa Zaadens hukunci daidai abinda sukai amma a gaban idonsa ta tarwatsa wannan damar sbd samarwa yan uwanta sassaucin da baya musu fata ko kadan. Tafasa da wani irin zafi kirjinsa ya dauka ya dago ya kalleta kallon dayake jin tana ficewa ransa shima kaman yanda take jin tsanarsa. Miqewa tsaye yayi yana kallanta da jajayen idanuwansa yace "Tinda da bakinki kin fada bakya buqata babu amfanin barin Zuciyar a kirjin naki tabbas zaa cire a sakawa wadda ta cancanta, Daman kashe wata akai dan rayaki kema ba illa bane dan kin tafi wani ya rayu" Qarasa kalaman yayi suna yankar zuciyarsa yanka me tsananin ciwon gasken daya sakasa dauke idanuwansa daga kallanta tsananin fushinsa da bacin ransa na bayyana. Zuba masa idanuwanta tai hawaye ba tsiyaya tana jin kalamansa har cikin zuciyarta sbd ayau ya gama bayyyanar mata da girman qin dayake mata da jininta, Numfashi ta sauke ahankali tana share hawayenta ta bude baki tace "Wallahi tallahi ni Jannah na Amince da yaddata ba tirsasawa ka cire Zuciyar dake kirjina ku dauki abarku" Mama data kasa cigaba da sauraron wannan kalaman na zallar baqin ciki da qunci ficewa tayi daga dakin tanajin duniyar na futa kanta itama gabaki daya hakama zuciyarsa na jin zafi da rashin kaunar ganin jannah wadda taketa kokarin hana zuciyarta qinta sbd ba laifinta bane amma zuciya batada kashi hakan na neman gagararta. Fitowa Jannah tayi idanuwanta jajir suna sake bushewa tabar asibitin tabi hanya tana tasa gurin zuwa ta nema bakin hanya ta zauna tana saka kanta a cikin qafafunta ta fasa kukan da batasan rayuwar da zataiba gwara ta zuciyar Ummitah ta huta itama da wannan masifun. Har dare tana gurin zaune bakinta da idanuwanta sun bushe qayau ta miqe ta nufi gidansu wanda yayi tsit ma kowa duka familynta dake rayuwar jin dadi da wadata a cikinsa yau an wayi gari babu kowannensu. A palo ta zube qasa kwance tana rintse idanuwanta sanyin tiles na ratsata, Bazata iya barin mahaifinta da dan uwanta da Ammar dasuka rage mata ba a duniya su shiga mummunan halin da zasu rasa rayuwarsu ba suma. Zata tsaya da duk abinda ya rage musu suke dashi ta yaqi AZIZ LIMBA akansu, Zata tsaya sai ta fidda yan uwanta a wannan masifar sbd bazata taba barin ya samu abinda yakesoba akansu, Ya samu iya fansarda dan haka ta isa haka sun biyasa harda qari dan haka lokaci yayi dazaisan tsananin qiyayyarta tinda iya soyayyarta ya sani. Miqewa tayi ta dakinta ta shige ta nufi toilet ta fada tana rufo kofar. Acan asibitin kuwa da zafin da radadin zuciya tabarsa... Sayd ma baisamu cewa komaiba kaman yanda mama takasa cewa komai sai jin datai tana son barin qasar ma gabaki daya ba asibitinba. Karfe goma sha biyun dare falaq ta bude idanuwanta ta saukesu akansa yana zaune gabanta ya zuba mata idaniwansa dukkanin sarewansa tana bayyana a fili. Lumshe idanuwanta tayi ahankali kafin ta miqa masa hannunta cikin rashin karfi ko kadan da karfin hali tana rufe ido ahankali. Miqewa yayi ya zauna bakin gadon nata yana dagota ahankali ya kwantar jikinsa yana rungumeta ahankali yana lumshe nasa idanuwan da sukai jajir yana sauke numfashi me dumi yana jin hutun da jannah ke fada shima shi yake buqata daga wannan rayuwar. Lafewa jikinsa falaq tai cikin sanyin ciwo da jiran lokaci ta bude bakinta ahankali itama tana fatar inama ace rayuwarsu ta baya duka ta dawo da bazata bari kudirin daukan fansa yayi consuming mahaifinta ba zasu barwa Allah komai allah yaji qan mahaifiyarta. Hawaye ne masu dumi suka gangaro mata suka sauka a gefen wuyansa yaji saukarsu har cikin ransa. Da muryan data ratsasa sbd sanyi da laushi da nutsuwa tace "Daddy karka manta a koyaushe babu abinda yakai zuciyar datake da yafiya da tawakkali nutsuwa da samun kwanciyar hankali, Ka kasance me banbanta kanka daga zama abinda wasu suka zama na rashin alkhairi, Ummitah rayuwarka ce a baya, Kafin Ummitah ka rasa mahaifinka ka tsaya kayi gwagwarmaya da rayuwa, Ka rasa mahaifiyarka ka tsaya kayi gwagwarmaya da rayuwa, Rashin Ummitah ya tabaka amma ka tsaya kayi gwagwarmaya da rayuwa dan haka a yanzu ma ka kasance me tsayawa kayi gwagwarmaya da rayuwa batareda ka gurbata jininka ko hannuwanka da jinin kowa ba, Zaadens sun cutatar da kai amma ni bazan taba so nawa mahaifin ya bari zuciya ta rinjayesa ta sakasa aikin da rayuwa zatai masa qunci a gaba kaman yanda taiwa zaadens, Banason ka bari kaunar dakake mun ta hallakar da kai, Ni na karbi kaddarata da hannu biyu zan jira kwanakin da suka ragemun su cika batareda kayi yunqurin komaiba da zai hallakar dakai....... Wani irin kuka ne yakeyi a jikinta yana qanqameta yana jin kalamanta na ratsasa suna kakkaryasa daga jarumtarsa ta shekaru, Itama kukan takeyi sosai mara sauti zuciyarta na karbawa ba daidaiba sbd baason kowane yanayinda zai taba zuciyar ta rasa sauran karfin daya rage mata na kwanaki. Sayd ne dayake bakin kofa yana jinsu ya silale qasa shima yana kuka tareda dafe knsa yana rufe bakinsa. Hawayenta ne suka qara gudu tana jin ciwon kukan da mahaifinta yake ayau me girma a jikinta basuda abinda zasu iyawa kansu sai yanda Allah yayi dasu. Tace "Daddy kamun Alkawarin zamu barwa Allah ikonsa, Kamun Alkawarin bazaka tirsasa jannah ko takurata ko saka kuka a fuskantaba, Kamun Alkawarin mun bar mata zuciyar Ummitah sbd Allah ne ya tsara zuciyar baa kirjin Ummitah zata rayu ba a zuciyar Jannah ne, Jannah na cikin tsananin quncin datake buqatan break daga wannan damuwar da babu ranar fita, Dan Allah inason kamun Alkawarin zatabarta ta zabi abinda take so da kanta wanda zai bata nutsuwa da kwanciyar hankalin zuciya, Ni nawa haqqin duka dayake kansu na yafe suji dana tsakaninsu da ubangijinsu, Inason Ayau Daddy kamun Alkawarin zakai freeing raka zuciyar daga dukkanin wannan quncin ka samu nutsuwar zuciya, Daddy dan Allah kada bari qunci yasake dabaibaye raywarka ko bayan tafiyana........ Karfin da kukansa yayi ne jikinsa na wata irin rawa da jijjiga ya saka nata kukan karfi itama tana jin zuciyarta na gazawa. Tari tayi me ciwon daya saka jini fesowa daga bakinta tana bata jikinsa da nata. Sayd ne ya shigo dakin da sauri yana yowa kanta Sbd AZIZ ya fita hayyacinsa kuka yakeyi sosai a jikinta kaman yaro a jikin uwarsa yana rokonta kada ta tafi tabarsa yayi mata dukkanin Alkawarin datakeso, Bazai sake waiwayan zaadens ba, Bazai sake tirsasa jannah ba koda rabuwa dashi ta zaba tabbas zai rabu da ita har abada. Sayd ta zubawa idanuwanta dake lumshewa tana bude baki zatai magana wani jinin ya sake zubowa wanda ya saka sayd din saurin rungumota jikinsa yana ambatar sunanta. Fiddausi ce data shigo taga yanda jaruman biyu ke kuka a jikin 'yarsu da kowannensu yake shirye da basa zuciyarsa akanta ta fita da gudu ta kira likita. Da gaggawa likitoci suka iso dakin aka janyeta daga jikinsu aka futar dasu. Mamace ta rungume su duka biyun a jikinta tsam tana rokon Allah ya kawo musu agajin gaggawa daga wannan musibar. Acan gida kuwa Jannah itama kwanan qunci tai idanuwanta basu samu bacci ba ko kadan mahaifinta dasu Maheer kawai take gani a idanuwanta tanajin tsoro na rufeta na yanda rayuwa zatai da ita. Washe gari tin 7 ta fita tafara yawon neman headquarters din da aka kaisu Dad. Har dare tana yawo bata gane komaiba ta dawo gida ta zube tana jin bazata sanyaya ba zataci gaba da nemansu. #MAMUH #BESTLOVE #BEST ROMANCE #BEST STORY #PATIENCE PLS MUTANENA #HOT LOVE IS COMING ZAFAFA BIYAR KALBIM 500 maZAFAFA BIYAR KALBIM 500 mamuhgee A DUNIYATA 500 Huguma AJIYA A DUHU 500 Billyn Abdul KIRJIN ME HANKALI 500 Miss xoxo Pay at 0022419171 AccessBank Maryam sani gummi Shedan biya 09033181070 Or mtn vtu at 09032345899muhgee A DUNIYATA 500 Huguma AJIYA A DUHU 500 Billyn Abdul KIRJIN ME HANKALI 500 Miss xoxo Pay at 0022419171 AccessBank Maryam sani gummi Shedan biya 09033181070 Or mtn vtu at 09032345899*_KALBIM_* _Mamuhgee_ 90 *UMMU_MAHNOOR LUXURIES* (Best luxuries shop) 08034469681 08135142610 Aslm Alaikm ina kuke masu neman luxuries na kayan alfarmar kece raini? Ina masu son su saka sitirar alfarma ta zamani ta manyan mata masu aji da zaa kalleki kallo daya asan sitirar alfarma e kika saka? Shin kunsan me ake nufi sa kayan asalin yan gayu da nuna gayu? Sitirar Alfarma kikeson sakawa? Sitirar da kike ganin manyan mata da ita? Sitirarda zakiyi gayun sallah dake da yaranki a dauka waje kikaje da kanki kika siyota? To kizo ga damarki ta sameki sbd UMMU_MAHNOOR LUXURIES ta kawo miki sauki har gida, Karkice se masu kudi ke iya siya har kema me yar dama zaki samu naki da saukin kudi kuma best quality da kalar zamani data yan gayu, Nidai Mamuh nace duk wadda ke son a buga gayun sallan bana da ita da 'yayanta to tazo gurin UMMU_MAHNOOR LUXURIES tai siyayyar sallanta harma zuwa gaba dan nasan zakuji dadi da fahimtar abinda nake fada akan kayanta💯💯 Abubuwan da zaki samu a gurinta with the best quality na wayayyun mata masu aji yan gayu sune; Atampopi Laces Shadda Materials Shoes Bags Veils Trolleys Jewellerys Oil perfumes Numbers 08034469681 08135142610 Handles Instagram @ummu_mahnoor_luxuries TikTok username @ummu_mahnoor_luxuries Facebook ummu_mahnoor_luxuri ************** Washe gari da karfin hali ta tashi ta shirya komai bata sakawa cikinta ba ta fice daga gidan ta nufi yawon nemansu wanda takejin idan bata gansu ba ta daukarwa ranta yawon garin kullum har ranar da Allah yasa ta samu ganinsu. Yawo tayi sosai yau dinma har dare babu wani haske ta dawo gida tanajin zuciyarta kaman bazata iya daukaba amma kuma bazata iya sadakarwa ba, Alkawari taiwa kanta na nemansu da gyara kuskuren da sukai tinda sun tuba, Hakama kome sukai ko zasuyi bazata iya gudunsuba, Bazata taba gajiya da nemansu da tsayawa kan neman yancinsu ba. Da daddaren wanka tai ta fito ta nufi kitchen batako iya tsayuwa daidai ko tafiya daidai gabobin jikinta duka sun gaji suna kuma nunawa, A kitchen din jollof rice kadai ta tarar wadda babu komai na proteins a cikinta sbd cefanen gidan sun qare babu me siya ita kuma bata zama. Kular abincin ta dauka tana silalewa qasa ahankali jikin bango ta zube qasa ta saka hannunta cikinsa tafara debowa tana sakawa bakinta. Wasu hawaye masu tsananin zafi ne da ciwo suka gangaro mata tanaci gaba da cusa abincin bakinta tana taunawa tana hadiyewa.... Kewace ta sakata fasa wani irin kuka me tsanani ciwo tana rintse idanuwanta, Kuka takeyi sosai tana cusa abincin cikinta, Kewar mahaifiyarta take, Kewar mahaifinta take, Kewar yayunta da ahalinta gabaki daya takeji, Yaya zata iya rayuwar nan ita kadai babu kowa? Tayaya zata iya rayuwa da radadi da ciwon dayake cikeda zuciya da kirjinta? Inama itace Ummitah data bar duniya tin komai bai lalaceba, Kukanta tsananta yakeyi tana ajiye abinci ta zube kwance tana kukan dayake amsawa a kitchen din gabaki daya tana qanqame jikinta. Dare sosai takai a hakan kafin ta dafa ahankali ta tashi zaune tareda daukan sauran abincin ta nufi fridge ta bude ta saka batareda tinanin ta riga ta saka masa hannu ba hakama kular dayake ciki ta juya tabar kitchen din ta koma dakinta ta shiga toilet tayo Alwala ta fito ta tayarda sallar nafila ta neman sauki da sassauci daga ubangiji. Ta jima tana salloli da addua kafin ta miqe batareda ta cire kayan sallar jikinta ba ta kwanta bakin gado a rakube tana qanqame jikinta tareda tina ranakun datake kwanciya a jikin mahaifinta cikeda kauna da kulawa xai ringa tarairayanta har lokacinda bacci zai dauketa tukuna ya rakota dakinta ta kwanta kamar qaramar yarinya. Hawayen da suka gangaro mata ne suka sauka a hannunta da kanta yake kai ta sauke numfashi ahankali tana rufe idanuwanta duk da tasan da wuya baccin yaxo. Baccin daukanta yayi kuwa wanda harya hanata tashin asuba sedai ta bude ido taga rana tayi sbd rabonta da bacci kusan tin rasuwar Mimi. Tashi tayi da sauri duk da batada wani kuzarin daya rage, Toilet ta nufa ta fada, Bata wani jimaba ta fito da alwala tayi sallah, Tana idarwa miqewa tayi ta sake komawa toilet din tayi wanka ta fito ta shirya ta fito ta fice daga gidan. Yauma kamar kullum ne amma ko kadan batajin zata gaji dan haka bata gajin ba ta a cikin kwanaki kadan ta zare da nema da yawon daya fatar da ita hayyacinta gabaki daya ta koma kalar tausayi, Ramar data sauya kamanninta tayi tana wani irin jemewa sbd damuwa da tinani da rashin cin abinci, Masu aikin gidan kaf sun fara tafiya harda securities sbd gidan dai ya zama tamkar fanko babu kowa babu motsin komai, Abinci ya qare babu me siya ba kudin siya, Asibitin Zaadens kuwa a ranar da aka kama su Dad a ranar aka rufeta tareda kama da yawa cikin ma'aikatanta da likitocinta harma da nurses. Dan haka gidan ya koma ba kowa a yanzu sai ita kadai da me aikinsu daya data kasa tafiya tabarta sbd tausayinta daya rinjayeta. Kwanaki sun fara tafiya shiru babu motsi ko maganar komai data fita akan case dinsu Dad dinta wanda a yanzu ta hakura da yawon ta zauna jiran ace wani abu sbd koman daren dadewa dai zaa fara shariar case din dan haka take jiran a motsa sbd tasan inda suke. A Limbas kuwa komai shirinsu na barin qasar ya kammala tsaf zasu tattara subar qasar su koma inda suka fito, Rayuwa tayi qunci sun rasa dukkanin dan farin cikin dasuke dashi, Sun rasa walwalarsu kaman yanda zaadens ke cikin qunci da baqin ciki suma a cikinsa suke sbd daga karshe Yaqin nema da daukan fansa ya sakasu a jirgi daya da zaadens sbd a yanxu dukkaninsu baqin ciki da qunci mara yankewa suke cikinsa wanda dukkaninsu suke fatan inama rayuwa zata dawo baya da kowa yabarwa Allah baiyi abinda yayi din ba. Dan haka su suka yanke runguman kaddara su koma suci gaba da rayuwa cikin abinda Allah ya kaddara musu Ba Ummitah ba falaq kila.... Itama Jannah a yanxu abinda take nema a rayuwa kawai shine ahalinta, Sun rungumi kaddara sun shirya karban rayuwar da ubangijinsu ya tsara musu a gaba, Zasu tattara su tafi inda zasu bude sabuwar rayuwar hakuri da dangana me tsafta tareda tawakkali. Karfe goma na dare tana zaune palon gidansu rakube cikin kujera ta rungume jikinta idanuwanta a rufe tsit babu motsin komai da kowa babu haske sosai sbd a yanxu gidan bako inane yakeda haskeba batason haske sosai duhu ne a ciki da wajen rayuwarta ta yadda ta karba hakan dan haka hasken lantarki ma bataso sbd baya haskaka rayuwarta. Yanda idanuwanta suke a rufe tayi nisa a quncin da batajin sautin komai saina baqin cikin dayake dabaibaye da rayuwarta. Ahankali taji qamshinsa yana shiga hancinta yana isa cikin zuciyarta, Qin bude idanuwanta tayi sbd tasan tinanine kawai irin na zuciyar dake dauke da sauran soyayyarda ta dade da mutuwa. Kamshin ne yake cigaba da shigar hancinta wanda ya sakata bude idanuwanta cikin sanyi ahankali batareda ta motsaba, Akansa idanuwanta suka sauka yana tsaya gabanta ya zare kaman yanda ta zare, Ya fita hayyacinsa kaman yanda ta fita, Ya sauya ya tashi daga AZIZ LIMBA ya koma uban da baida iko baida abinda zaiyi dan cetan rayuwar yarsa sedai saka ido yana kallanta tana rasa rayuwar ahankali har zuwa ranar karshe da ranta zai fita daga gangar jikinta.. Zuba masa idanuwa tayi har lokacin bata motsa ba kallansa kawai take kanta na daga kwance a hannuwanta... Shima kallanta yake batareda ya motsa ba ko furta komai ya zauna gefenta ahankali tareda zuba mata ido itama har lokacin idanuwanta na kansa tana kallansa cikeda sanyi da mutuwar jiki. A rayuwa idan akace soyayya to azaba na tattare a cikinta sbd ita a tata soyayyar azaba da qunci tareda radadi sune suka cike tata soyayyar, AZIZ LIMBA tabbas soyayyarsa itace jarabawar rayuwarta ta farko da batajin zata fita har abada, Tana sonsa,tana tsananin sonsa,tana kaunarsa,tana tsananin kaunarsa, Tana sonsa,tana sonsa,tana sonsa,tana kuma qara sonsa........ Hawaye ne masu radadin dayake cikin zuciyarta suka gangaro gefen idonta suna sauka a hannuwanta da fuskanta ke kai ta lumshe idanuwanta ahankali ta sake budesu akansa har lokacin bata motsaba bare furta komai. Ja shima nasa idanuwan ke qarawa sbd nauyin da kirjinsa ke qarawa yana kallan hawayenta dake sauka wanda yasan na Soyayyar dake wahalar dasu ne wadda haryanxu ya kasa yadda da ita bare furtawa... Ahankali ya ciro hannuwansa ya ajiye abinda yake hannunsa gefenta yana maida kallansa kan passport dinta wanda ta bari ranar dataje dauka a limbas dayake hade da ticket. Gangaro da idanuwanta tayi a hankali zuwa kan passport din nata da shima yake kalla ta motsa hankali tareda miqa hannunta ta dauki passport din tareda ticket din ta budesa ahankali ta zubawa ticket din idanuwanta wani Yanayi me nauyi yana danne kirjinta ta dago ta zuba masa idanuwanta da suka sauya zuwa ja me ciwo ta bude bakinta ahankali cikin sanyi tace "I love you ABDULAZIZ AY LIMBA, I Love you morethan wat Ummitas heart can take, I love you morethan anyone in this lifetime, I love you ABDULAZIZ LIMBA....." Hawaye ne suka gangaro mata daga jajayen idanuwanta ta zubawa nasa idanuwan da suka cika da wasu irin hawayen da radadinsu yake fitowa daga zuciyarsa sbd kalamanta kashesa sukeyi suna yanka dik wata jijiyan jikinsa yana jinsu har cikin ruhi da zuciyarsa... "AZIZ LIMBA Zuciyata na maka soyayyar datai karfine sbd Zuciyar Ummitah dake kirjinsa da kuma soyayyar da kaina nake ma, Duk illar da kayiwa rayuwata zuciyar datake kirjina bata dena sonka ba sbd wannan soyayyar da ita zuciyar ta rayu kuma zataci gaba da rayuwa sedai kuma karka manta ni jinin Zaadens ce, Bazan taba tsallake ahalina na zabi rayuwa da kaiba duk son da zuciyata ke maka." Ticket din ta zare ahankali daga cikin passport din ta yagasa cikin sanyi ta zubar a tsakiyarsu ta rintse idanuwanta hawayen dake ciki suka gangaro tace "AZIZ LIMBA na zabi ahalina, Na bar limbas, Na hakura da auren Limbas dayake kaina, Na zabi rayuwa batareda kaiba na zabi familyna a kowane hali suke ciki zan tsaya tareda su ina fatan kowannenmu ya samu abinda rayuwa zata daidaita masa a gaba" Katseta yayi ta hanyar kama hannuwanta duka biyu da nasa hannuwan yana buki zaiyi magana ta zame hannunta daya ta rufe masa baki da tafin hannunta tana girgiza masa kai sbd har cikin zuciyarta ta ciresa ta hakura ta zabi familynta sbd har abada shi da ahalinta bazaa taba zamowa daya ba dan haka gwara kowa ya zaba nasa yayi rayuwarsa. Hannunsa ya dora akan nata yana bude baki Ahankali da nauyi a muryansa sosai yace "Nayiwa falaq Alkawarin bazan taba tirsasaki ba har abada, Alkawarinta ne akaina wanda bazai taba barin nayi miki dole ba hakama na alkawarine akaina na cika miki zabinki batareda tilastawa ba, Karki zabi abinda zai kawo karshen rayuwarda baa riga ma anfaraba, Ki......." Katsesa tayi ta hanyar girgiza kanta hawaye masu zafi na tsananta gudu akan fuskanta ta bude baki muryanta na bayyanarda tsananin radadi tace "Na zabi ahalina har a yanzu, Bazan taba barinsu na bika ba AZIZ LIMBA, Na zabesu,zan kuma sake zabarsu,zanci gaba da zabarsu har karshen rayuwata" Qarasa maganar tai kuka me tsananin ciwo na zuwar mata ta soka kanta cikin qafafunta tanayinsa ahankali zuciyarta na tsananin ciwo da radadi me girma. Shima radadi me zafi da ciwon gaske kirjinsa ke masa idanuwanta na qara wani irin jajir hannuwansa suka fara rawa ya miqe ahankali baice komaiba ya nufi kofa ya fice yana sakawa ransa zai bata yancin datake so na har abada sbd Allah dai ya nufa alaqarsu ta qare daga nan, Hakama rabuwa da ita a yanzu shine mafi alkhairi garesu su dukan sbd a duk lokacinda ya kalli halin da falaq take ciki jin yakeyi kaman bazai iya hakura da abinda Zaadens sukai masa ba zai iya kashe daya daga cikinsu dan raya tasa 'yar shima dan haka nesantar junan shine mafi alkhairi garesu duka suna buqatan break daga wannan masifar ta rayuwa. #MAMUH ZAFAFA BIYAR KALBIM 500 mamuhgee A DUNIYATA 500 Huguma AJIYA A DUHU 500 Billyn Abdul KIRJIN ME HANKALI 500 Miss xoxo Pay at 0022419171 AccessBank Maryam sani gummi Shedan biya 09033181070 Or mtn vtu at 09032345899*_KALBIM_* _Mamuhgee_ 91 *SHOP WITH ME by RANO* 08030811300 Best children's clothing shop💯 https://chat.whatsapp.com/Gk4H76TlRgyAAWIWgx3Jo7 Kina neman in da zaki samun kayan yara classy kaya na yan gayu at a very affordable price? Ko kina son fara kasuwancin kayan yara amma baki da jarin da zaki saro kayan? Nesa ta zo kusa, kiyi joining community din nan muna saka kaya masu kyau available da inganci a farashi me sauki da zaki dauka ki tallata har ki samu naki kema. Burinmu shine kowacce mace ta samu sanaar da zata dogara da kanta. ************* Yana ficewa daga palon koda ya isa mota ko gani bayayi sosai kirjinsa tsananin ciwo yakeyi da sauri Sayd ya bude masa mota yana kasa kara kallansa sbd yanayinsa dayake a munane. Barin gidan sukai yana dafe kirjinsa dake neman bugawa radadin gaske yakeji yana kasa riqe ciwon yafara neman numfashinsa dayake yankewa yana damqe hannuwansa da karfi idanuwansa na kasa riqe azabar kirjinsa nasa... Itama yana ficewa ta zabe qasa ta zube tana fasa wani irin azababben kuka me kargin gaske tana dafe kirjinta dayake mata tsananin ciwon dayafi na koyaushe tana jin kaman zata mutu.... Har cikin ruhinta take jin azabar da kirjinta keyi tana tsananta kukan da batada me rarrashi, Batada wanda zai ko tsaya akanta ta samu sassaucin qunci da ciwon datake ji a lokacin na zabar rabuwa da namijin ta jure komai akansa, Inama tin farkon haduwarta dashi ta jure ta danne sonsa da bata iso wannan matakinba da ayau take jin inama tabar duniya. Su kuwa suna isa gida kai tsaye bangarensa ya wuce batareda ya bari kowa yaga yanayin dayake ciki ba yana shiga tin a kofa ya zube qasa yana dafe kirjinsa dayake masa azabar dabazai iya daukaba, Wasu irin hawaye ne suka gangaro daga idanuwansa masu tsananin zafi yana zubewa qasa kwance har lokacin hannuwansa na dafe da kirjinsa.... A daidai wannan lokacin Sayd ya shigo sbd tin a mota ya lura da yana cikin mummunan hali.. Sayd na shigo wani irin jini na fesowa ta bakinsa me karfin gaske idanuwansa na rufewa..... Cikin matsanancin tashin hankalin daya saka kafafunta Sayd sarewa ya isa garesa da rarrafe hannuwansa na rawa ya ambaci sunansa da karfin daya saka duka jamaar gidan fitowa. Mama na ganin AZIZ din da jini kasa qarasowa tayi itama jiri ya debeta ta zube a inda take. Shi kansa Sayd bazai iya tuqi ba sbd mummunan halinda ya shiga dan haka ambulance aka kira babu dadewa sosai ta iso aka kwashesa zuwa asibitin harma da mama wadda itama manyanci da ciwon damuwa suka hade suna neman qarasata. Fiddausi da Sayd ne a tsaye kawai kaf familyn sai baba alhassan wanda shima dole damuwa ta tada nasa jikin da ake lallabawa. Se cikin dare aka samu Bugun zuciyarsa da numfashinsa suka dawo daidai sedai shima take ciwo ya qarasa maidasa abin tausayi sbd baisan waye ma yake kansa. Sayd da damuwa take neman kashesa shi kadai tini ya qarasa hada kan komai nasu a cikin kwana biyu ya gama handling komai akai sabbin presidents da chairmans da directors a companies dinsu ya qarasa handing over na komai ga latif, Securities ma da masu aiki na Mansion din dukkaninsu babu wanda baa bawa manyan kudaden da zai jima bai nemaba aka sallamesu duka kowa da kowa. Washe gari zasu tafiyarsu subar qasar dan haka a daren Motar Sayd ta tsaya a kofar gate din Zaadens ya fito mota ya bude gate da kansa ya shigo sbd babu securities kamar zaadens din baya sai mai gadi daya wanda shima ya kasa tafiya ne yabar jannah kaman yanda me aiki daya ta tsaya shima tsayawa yayi. Harabar gidan a kwai haske amma kamar baya ba, Sanyi jikinsa yayi shima sosai farkon zuwansu Zaadens na dawo masa a lokacinda kowa na cikeda lafiya da kwanciyar hankali da burirrika amma ayau dagasu har su din kowa ya rasa abubuwa da dama da har abada bazasu taba dawowa ba. A kofar palon ya tsaya ya miqa hannunsa ahankali yayi knocking idanuwansa jajir. Shiru babu motsin kowa, Sake bugawa yayi yana dan ja baya kadan...shiru baa budeba dan haka ya sake bugawa yana ci gaba da bugawa a natse cikin sanyi. Shiru kusan tsawok lokaci me tsayi, Ajiyar zuciya da numfashi me zafi ya sauke yana juyawa xai bar gidan aka bude kofar ahankali cikin nutsuwa da sanyi. Me aikice ta bude kofar cikin fargaba a sanyaye. Juyowa yayi ya kalleta itama shi take kalla cikeda damuwa. Bude baki tayi tace "Barka da zuwa" Amsawa yayi yana sauke kallansa daga kanta yace "Ms jannah nakeson gani" Shiru tayi tsawon seconds kafin tace "Batada lafiya amma bismillah bari na sanar mata" Shigowa yayi ya zauna a natse a palon kansa qasa idanuwansa har lokacin jajir. Wucewa tayi ciki ita kuma zuwa dakin jannah dake kwance shiru idanuwanta rufe. Bude dakin tayi ahankali ta shigo da sallama me sanyi sbd tasan ko tayi knocking jannah bazata iya maganar cewa ta shigoba bare tasowa ta bude din. Cikin nutsuwa da sanyi tace "Sir Sayd daga Limba yazo yana son ganinki" Bude idanuwanta tayi ahankali batareda ta motsaba. Sake maimaitawa me aikin tayi kafin ta juya ta fice daga dakin. Shiru shiru bata fito ba tsawon lokaci kafin ta bude dakin ta fito sanye da doguwar hijab har qasa fuskanta ta rame sosai tayi haske sosai. A hankali ta tako ta iso palon ta zauna a natse batada karfi ko kadan sbd ciwon dayake tattareda ita tsawon kwanakin. Nunfashi ya sauke ahankali sbd shiru sukai dukkaninsu babu wanda yace komai. Dagowa yayi Ahankali ya kalleta zuciyarsa na cika da damuwa me tsanani gaske ya zura hannunsa cikin aljihun qatuwar jacket din dake jikinsa ya ciro daguwar envelope din datake sealed ya miqe ahankali ya isa gabanta ya ajiye mata muryansa na wata irin sanyi me tsananin gaske sbd damuwar datake rinjiyarsa yace "Daga AZIZ LIMBA......."" Rintse idanuwanta tayi ahankali wani mashi me tsananin zafi na sukar tsakiyar kirjinta ta dora hannunta akan kirjin ahankali tana karban azabar datajin da dukkanin imaninta kafin ta miqa hannunta dayake rawa ta dora akan tanardar ta dauka tareda dago idanuwanta da sukai jajir ta kalli Sayd din ta bude baki Ahankali tace "Thank you for everything" Rintse idanuwansa yayi yana juyawa ya fice yana fatar Allah ya kawo musu sassauci su duka. Yana ficewa damqe takardar tayi a cikin hannunta tana son fashewa da kuka amma sam babusa hawayen sun qafe sai jajayen ido. Miqewa tayi daqyar tana hada hanya bata gani ta isa dakinta ta daga takardar tana son budewa ta karanta yanda aurenta ya mutu amma idanuwanta ma ganinsu daukewa yayi jin take tana neman mutuwa, Da rarrafe ta isa gurinda jakarta take ta bude ta saka takardar a ciki tana zamewa qasa.... Idan lissafinta yaje daidai a date din dayake jikin ticket dayazo dashi a ranar gobe ne tafiyarsu tafiya ta har abada ba dawowa kila. Silalewa qasa tayi yana kwantawa tareda rufe idanuwanta ahankali tana hadiye duk wani qunci da ciwo. Karfe goma sha biyu saura Ta isa asibiti a lokacin data san babu kowa a asibitin tareda Falaq sai Fiddausi. Ko data isa itama a cikin ciwo da rashin karfi take amma zuciyarta na tsananin son yiwa falaq ganin karshe.. Tana shiga dakin Fiddausi dake zaune ta gama sallah tana addua tana ganinta ta miqe da sauri suka rungume juna tana fashewa da kuka itama jannah din fashewa da kuka tai tana kallan fuskan Falaq data koma kaman babu nama a cikinta anma rufeta sosai baa wani budewa. Sosai suka jima a hakan kafin jannah ta isa ga Falaq ta rungumeta ahankali tana shafa fuskanta tana kuka sosai hawayenta na lalata fuskanta gabaki daya. Bakinta takai tayi kissing gefen fuskan falaq din kafin tayi kissing goshinta shima tai kissing hannunta da kafunta tana jin kamar ta bude kirjinta ta ciro zuciyar dake ciki ta bawa falaq din.. Kamar a mafarki falaq ta bude idanuwanta da basa gani sosai ta kalli fuskan jannah din idanuwan suka koma suka rufe. Fiddausi ce ta sake sanar da ita zasu tafi ne ba lallai Falaq ta samu donor ba dan haka sun hakura sun barwa Allah komai. Kasa cewa komai tayi bayan kukan datakeyi tana sake kissing falaq tako ina tana mata addua tamkar uwar data haifeta tareda mata fatan nasara da saukin da duk Allah yasan shine rahama gareta. Ko data fice daga dakin bata sake waiwayowa ba har tabar asibitin ta nufi gida tana sakawa kanta dangana. Ko bayan isarta gida bata rintsa ba yanda taga rana haka taga daren har gari ya waye tayi sallah ta koma ta zauna ta zubawa agogo idanuwanta da sukai jajir tana bin kowane second da agogon ke bugawa har lokacinda karfe 11 na rana tayi wanda shine lokacinda jirgin ahalin Limbas gabaki daya zai tashi daga qasar Nigeria sunyi tafiyarsu bayan sun bar komai zasuje su fuskanci sabuwar rayuwa a duk yanda zatazo. Lumshe idanuwanta tayi lokacinda sha daya din ta buga a kan idaniwanta tanajin wani nauyi ya tsaya cak a tsakiyar kirjinta wanda ya tsaya kenan bazai saukar mata ba har abada ta sani. #MAMUH ZAFAFA BIYAR KALBIM 500 mamuhgee A DUNIYATA 500 Huguma AJIYA A DUHU 500 Billyn Abdul KIRJIN ME HANKALI 500 Miss xoxo Pay at 0022419171 AccessBank Maryam sani gummi Shedan biya 09033181070 Or mtn vtu at 09032345899*_KALBIM_* _Mamuhgee_ 92 *SHOP WITH ME by RANO* 08030811300 Best children's clothing shop💯 https://chat.whatsapp.com/Gk4H76TlRgyAAWIWgx3Jo7 Kina neman in da zaki samun kayan yara classy kaya na yan gayu at a very affordable price? Ko kina son fara kasuwancin kayan yara amma baki da jarin da zaki saro kayan? Nesa ta zo kusa, kiyi joining community din nan muna saka kaya masu kyau available da inganci a farashi me sauki da zaki dauka ki tallata har ki samu naki kema. Burinmu shine kowacce mace ta samu sanaar da zata dogara da kanta. ************** Zamewa tayi ta kwanta ahankali tana rufe idanuwanta tana karban sabuwar kaddadarta daga yanxu da Limbas suka barsu kwata kwata har abada. "AZIZ LIMBA haduwa da kai da shigarka xuciyata shine abu mafi dadi da samun gamsuwan zuciyar dazan samu har abada dan haka ina maka fatan alkhairi tareda samun dukkanin farin cikin rayuwa da abinda kakeso" Wannan kalaman sune abinda zuciyarta take fada Wunin ranar ko bakin kofar dakinta bata fitoba tana daki a kwance sallah kawai ke tadata a sanyaye sbd ko karfin jiki batada. Abinci daya aka kawo mata ta tashi xaune duk da bata iya ci amma hakanan ta cusawa cikinta ci idanuwanta jajir ta gama ta koma ta kwanta. Har dare haka take har safe bata rintsa sai guraren yamma washe gari ta fito ta cusawa cikinta abinci da ruwa ta samu karfi ta fice yawon neman su Dad. Sai dare sosai ta dawo tai sallah ta nemi guri ta kwanta. Washe gari batada mai batada kudin da zata sakawa motar mai dan haka ta nufi dakin dad tayita neman key din tasa motar ta samu ta dauko da ita ta fita tayita yawo sai dare ta dawo ko ranar. Sake dawo da yawon nemanta ta cigaba dayi ba dare ba rana wanda ya saka duka mayukan dake cikin motocin gidan suka qare ta koma neman yanda zata cire kudi a acct din dad da Maheer ko mimi ko Ammar amma dukkaninsu babu Atm card sbd sam basa amfani dashi banki ake zuwa a ciro musu kudi a manyan jaka a kawo musu haka suke, A lokacin da suna Germany ne suke amfani da cards da sauransu amma anan basu damu da wannan ba kudi ake ajewa sababbi marasa nauyi dauka kawai kakeyi ka zuba aljihu ka fita ko jaka. Rasa yanda zatai dan haka kai tsaye ta siyar da motarta cikeda quncin rashin masifar da zata taimaka musu ga abinci suna nema. Bata iya siyayyar abinci ba dan haka mai aikin ta bawa duka kudin bayan ta cika motocin gidan da mai tace tayo siyayyar komai na abinci da suke buqata. Bayan fitarta mai aikin kallan tarin kudin da suke hannunta tayi masu yawan da bata taba riqewaba rayuwarta sbd abinci ne me yawa jannah tace ta siya wanda zasu dade sosai da sosai basu nema ba... Shedan ne ya fara gurbata mata tinaninta akan lokacin tafiyarta itama yayi dan haka dakin mimi ta nufa ta tattara dukkanin yan sarkokinta da abubuwa masu tsadar gaske ta fito ta tattara kayanta da wanda ba nata ba ta fito ta fice ta samu mota tai tasha kai tsaye sbd barin garin. Sai dare jannah ta dawo gidan bataji motsinta ba ta dauka tayi bacci ne dan haka itama shigewa tai kawai. Da safe tana fitowa kitchen ta fara nufa taga alamar babu wani abu da akai a kitchen din tin jiya sbd komai a bushe ba alamar ma an shigo tin jiyan. Store ta nufa taga babu komai wayam alamar baayi siyayyar ba, Fitowa tayi a sanyaye ta nufi dakin me aikin ta bude taga babu komai nata ta kwashe sai tarkace kawai. Fitowa tayi ta nufi dakin Mimi ta duba taga duk an yamutsashi an kwace sarkoki da wasu abubuwan harma da sitirarta aka kwasa. Numfashi me dumi ta sauke ahankali tanajin jikinta na sanyi sbd ta fahimci abinda ya faru matar ta gudu kenan sbd kudin. Palo ta dawo kafafunta na sagewa ta zauna tana tallafe fuskanta da tafin hannuwanta. Batasan matar na son kudi ba da zata siyar da abubuwa da dama ta bata kudin sbd ta zauna da ita ta sabu da ita a yanzu kuma ta sake komawa ita kadai a rayuwarta me aikin ma datake tayata quntacciyar rayuwarta ta gudu ta barta. Ta dade a gurin zaune kafin ta miqe ta nufi daki ta sako hijab ta fito ta fita gidan a hanya taje ta siya abinci ta xauna cikin mota tana ci tana jin kaman zai shaqeta ta mutu sbd kwata kwata ba abinci ne a rayuwartaba kawai cikinta takeson abincin ya shiga sbd kada ta rasa karfin tsayuwa da kafafunta ta taimaki iyayenta. Wani abincin ta sake siyowa ta dawo dashi gida ta bawa me gadi kudi shima tace ya ringa cin abinci. ********Sati Biyu da tafiyar me aikinta tana kokarin fita da safe motocin jamian tsaro suka iso gidan tareda zungureriyar takardar karbe komai na Zaadens komai da komai hatta siritar sakawansu sbd zaa fara shariarsu dan haka ana buqatar dakatar da komai nasu har sai yanda shiriar ta kaya dan anason kaf rayukan da suka dauka sai anbiya diyyarsu me girma. Zamewa tayi jikin bango tana rintse idanuwanta da kuka ya qafe musu tana sauke numfashi tareda ambatar sunayen Allah a cikin rant. Da kansu suka shiga suka rufe koina ita kadai aka bari ta dauki kayan sakawarta a cikin yar qaramar jaka ta fito suka karbe keys na duka motocin gidan ana rubuce rubuce da daukan hotinan komai. Dakin me gadi da aka sallama take aka bata damar zaunawa har a gama komai ita duk bata damu da wannan ba nutsuwa taji tana samu na fito da iyayenta da zaayi a fara shariar sbd tasan a wannan lokacin Allah ne kadai yasan irin azabar da suke cikinta. Washe gari tinda safe ta shirya da dan sauran canjin dayake hannunta ta fito dakin me gadin tareda rufe kofar dakin ta fice gate ta rufesa shima tafara tafiya me dan tsayi sosai kafin ta samu abin hawan dazai kaita inda daga karshe aka sanar da ita suna can bama a cikin garin abuja bane fita akai dasu. Headquarters din da zaa taho dasu ta nufa tana isa sauka tayi ta nemi guri ta rakube ta zauna tana jiran a iso dasu. Tinda ta iso ake kyararta ana mata wasu tambayoyi masu ciwo da wulaqantawa bata cewa komai sbd jikinta rawa ma yakeyi na tsoro amma kuma zuciyarta ta riga ta bushe ta kafe akan ahalinta dan haka ta kasa bari tsoronta ya rinjayeta ta gudu daga gurin. Zaman awa daya tayi idanuwanta duk sun qanjame bakinta ya bushe zuciyarta harbawa takeyi sosai tana zubawa hanya ido., Kunnuwanta ne suka fara jiyo mata jiniya wadda ta saka yan media dake boye fitowa da yawansu suna cike kofar shiga gurin da yan kallo sosai harma da yawa daga cikin familyn wainda aka kashe nasu na nan Nigeria sbd an bayyanarda da sunayen wasu daga cikinsu sosai a yanda labarin ke yawo.. Miqewa tayi tsaye tana fitowa inda ta rakube kanta bugun zuciyarta na tsananta tana kafe motocin da idanuwanta har suka tsaya aka bude bayan motar prison din, Dr Ken ne wanda ya rasa kafarsa daya aka fara fitowa dashi gabaki daya kammaninsa sun sauya ya koma kamar mahaukaci idonsa daya ya tsiyaye. Dauke idaniwanta tayi akansa sbd bashi take buqatan gani ba, Ammar ne na biyu wanda yanda ya koma ya sakata yin baya tana neman faduwa zuciyarta na kasa dauka sedai kafin ta ja wani numfashin aka fito da Dad dinta wanda ta ambaci sunansa da karfin gaske tana yi kansa da tsananin gudu wanda ya saka duka jamian tsaro da yan media dawa da kallansu akanta hakama kafin jamian tsaro suyi yunqurin tareta da sauri tini ta isa kan mahaifinta ta fada jikinsa da karfin gaske sukai baya zasu zube sbd baida karfi ko kadan Ammar dayake tsayuwa da qyar da sauri ya tsaya bayan Dad din yana taresu ta qamqame dad da wani irin karfin gaske wanda shima duk da baya gani sosai sbd azabar dasuke cikinta wata irin runguma yayi mata me karfin gaske yana cewa "Jannah kece????? Qanqamesa ta sake yi da karfin gaske tana ambatar sunansa kawai zuciyarta kaman zata tarwatse a gurin ta fasa wani irin kuka me tsanani karfin gaske tana kiran sunansa kawai bata iya cewa komai tana jin kaman Allah ya dauki ranta a gurin a jikin mahaifinta. Shi kansa da baya ganinta sosai qanqameta yakeyi yana ambatar sunanta hannuwansa na tsananin rawa bakinsa ma na rawa.. Ammar ma juyawa yayi yana kasa kallanta kuka me karfin gaske yana zuwar masa kaman yanda Maheer ma kasa kallanta yayi kansa n qasa idanuwansa sunyi jajir. Securities mata aka kira da sauri suka fito aka fara banbareta daga jikin dad dinta ta sake qanqamesa tana qin sakinsa tana tsananta kukanta tana kiran sunansa. Kasa cireta daga jikinsa akai zuwa lokacin shima kukan yakeyi sosai sbd gabaki daya zuciyarsa matacciya ce akan 'yarsa.. Dukanta Securities din suka farayi tana qin sakinsa dan haka suka fara tsanantawa Ammar ya juyo da saurin yana rufeta jikinsa hakama Maheer dad ya rufe wanda shima ake dukansa sbd rufesu da duka akai ana kokarin rabasu jannah na sake riqe dad din wanda yake banbareta da jikinsa shima sbd a dena dukanta. Ba tausayi aka rufesu da duka gabaki dayansu dan haka Dad ya saka karfinsa ya cinketa daga jikinsa akai saurin riqeta tana zubewa qasa cikin tsananin kukan dayake neman qare mata tana rintse idanuwanta bakinta na fidda jini. Jansu akai zuwa ciki da karfi kowannensu bakinsa da hancinsu na fidda jinin dayake kona zuciyarta yana kasheta ahankali. Sai alokacin aka fito da Anny da dr Abraham wanda zaa miqa kasarsu acan xai karba nasa hukuncin sbd acanma sun kashe rayuka akai ciki dasu Anny bata iya ko tsayuwa sbd daurin dayake hannuwa da kafafunta. Ana shigewa dasu aka saketa tareda barinta zaune a gurin tana kukan da babu sauti sai numfashi kawai. Duk yanda taso sake ganinsu baa bata damaba dan haka a gurin ta wuni sai dare ta koma gida zazzabi me karfi na cinta. Kwantawa tai kawai bata iya komai sai jikinta dake rawar zazzabi har wani azababben bacci ya dauketa a gurin. Tsakiyar dare cikin bacci taji motsi a kofa ta bude idanuwanta ahankali daqyar sbd nauyinsu ta motsa tareda dafawa ta tashi zaune ta miqe tsaye tareda nufar window datake jin motsi kullum tinda ta dawo kwana dakin kullum tana jin motsi kaman akwai wanda yake kwana kofar dakin dan haka yau bude window tayi kai tsaye. "SALEEM" ta furta cikin tsananin sanyi da mutuwar jiki tareda kasa yadda da abinda idanuwanta suke nuna mata. #MAMUH ZAFAFA BIYAR KALBIM 500 mamuhgee A DUNIYATA 500 Huguma AJIYA A DUHU 500 Billyn Abdul KIRJIN ME HANKALI 500 Miss xoxo Pay at 0022419171 AccessBank Maryam sani gummi Shedan biya 09033181070 Or mtn vtu at 09032345899*_KALBIM_* _Mamuhgee_ 93 *SHOP WITH ME by RANO* 08030811300 Best children's clothing shop💯 https://chat.whatsapp.com/Gk4H76TlRgyAAWIWgx3Jo7 Kina neman in da zaki samun kayan yara classy kaya na yan gayu at a very affordable price? Ko kina son fara kasuwancin kayan yara amma baki da jarin da zaki saro kayan? Nesa ta zo kusa, kiyi joining community din nan muna saka kaya masu kyau available da inganci a farashi me sauki da zaki dauka ki tallata har ki samu naki kema. Burinmu shine kowacce mace ta samu sanaar da zata dogara da kanta. ************** Dakatawa yayi cak daga kokarin barin gurin dayake tareda kasa juyowa yana rintse idanuwansa da sukai wata irin rama suka qanjame., Bude kofar dakin tayi ahankali zata fito takarda me tsayin gaske ta fado daga jikin kofar wadda ta sakata dakatawa tana kallan takardar kafin ta dago ta kalli bayan saleem din wanda da alama shine ya saka mata ita Durqusawa tayi ahankali ta dauka tareda budewa hannuwanta na rawa tafara karanta abinda yake ciki..... Subucewa takardar tayi daga hannunta cikin wani irin slow na mafi munin tashin jiri ya dibeta tayi baya zata zube ya juyo da sauri ya tareta jikinsa yana sauke idanuwansa akanta. Numfashi ta ringa saukewa ahankali ahankali tana jero ajiyar zuciya tana samu tana neman karbo hankalinta dayake barin jikinta, Karfi ta harhada ta zame daga jikinsa tareda miqewa tsaye daidai ta daga hannu cikin rufewan ido ta sakar masa wani lafiyayyan mari tareda cakumosa bakinta na rawa hawaye masu tsananin zafi na gangaro mata tace "Me nayi maka zaka mun hakan??? Mene nayi na cancanta wannan abinda zakamun?? Idan ka zabi barina me zaka cewa ubangijinka da nauyina a yanzu ya dora maka? Me nayi dazan cancanci hakan? Sakinsa tayi tana yin baya tana neman kuka amma ya kasa zuwa tace "Ka tausayawa maraicina karka mun haka Saleem, Kai kadai gareni a yanzu, Mutuwa zanyi idan ka aikata abinda kake niyar aikatawa, Karka mun hakan, Dan Allah karka mun hakan saleem karka kasheni" Rungumeta yayi da karfi yana fasa kuka a jikinta yana girgiza mata kai cikin radadin zuciya yace "Mutuwa zanyi kamar yanda Mimi ta tafi, Zuciyata ta dade da bugawa banda sauran amfani a rayuwata yanzu bayan na bawa falaq zuciyata sbd nemawa ahalinmu sassauci da samun yancin fitowa daga azabar da suke ciki, Babu wanda zai iya janyewa ya kashe case dinnan su Dad su futo idan ba AZIZ LIMBA ba" Girgiza kai takeyi da karfi tana qanqamesa kaman zata shige kirjinsa ta boye zuciyarsa... "Jannah su Dad bazasu taba fitowa kashesu zaayi kaman yanda suka kashe wanda rayuwarki ce zata mutu ta lalace kwata kwata idan hakan ta faru, Banda amfani,banda tinanin kaina,banda iko ko karfin da zan baki kariya dan hakanne na zabi zama donor din Falaq Aziz sbd kubutar da Dad da Ammar wainda zasu baki kariya da karfinsu da rayuwarsu......" "No,no,no,no Saleem,pls pls pls dena fada, Bazan taba barin hakan ba koda zan rasa raina bazan taba barin kayi hakan ba, Falaq zata rayu,zata samu Donor, Zan bata tawa amma dan Allah Saleem karka mun hakan, Karka zabi barina a wannan quntacciyar duniyar ni kadai banda kowa sai kai, Karkayi Saleem kaine sanyin zuciyata a yanzu,kaine gani na da jina dan Allah karka barni ina buqatarka,ina tsananin kaunarka mutuwa zanyi idan kayi hakan" Gabaki daya ta fita hayyacinta batama san me take fada ba tana qanqamesa da karfi koina jikinta na wata irin rawa tana neman zarewa gabaki dayanta. Rawa shima jikinsa yakeyi yana janyeta jikinsa amma sam taqi sakinsa dan haka ya koma da ita ciki suka zauna taja jikinsa tanata surutai bakinta na rawa hakama jikinta. Rarrashinta yafara kokarin yi yana tattaro karfin hali sbd tagama kashe zuciyarsa da jikinsa da yanayinsa da yanda ta fita hankalinta fit lokaci daya da jin abinda zaiyi din. Shiru sikai yana shafa bayanta ahankali yana mata karatun adduoi a cikin kunnenta ahankali suna ratsata kafin ya fara karantu alqurani a cikin kunnen yana samar mata da nutsuwa da dawowa hayyacinta sbd alamun zarewa da suka bayyanar mata. Ratsata karatun keyi tana sakewa a jikinsa tana rufe idanuwanta ahankali ahankali har dare ya sake ratsawa sosai kamar wadda akayowa aiken bacci sai gashi ya dauketa ahankali ajikin Saleem din wadda yake kuka sosai yana mata karatun har lokacin. Duk yanda yaso yaci karfin zuciyarsa kasawa yayi sbd yanason kubutar da ahalinsa su rayu sbd rayuwar jannah din kawai, Hakama yanason ya bawa AZIZ LIMBA hope na sabuwar rayuwar daya rasa ta hanyar bawa falaq KALBIM dinsa a lokaci daya kuma ya biyasu zuciyar Ummitah da suka lalata musu komai akanta. Zare jikinsa yayi daga nata tareda kai bakinsa yana wani irin kuka me tsananin gaske mara sauti yayi kissing goshin jannah din ya rufe mata jikinta da doguwar hijab dinta tareda ciro dukkanin abinda yake jikinsa na dan kudaden dayake gararin samu ya ajiye mata ya fice daga dakin tareda rufewa ya bar gurin yayi tafiya me nisa kafin ya samu guri ya shige ya zube qasa yana wani irin gunjin kuka har asuba tukuna ya fito ya wuce yabar anguwar gabaki dayanta. Karfe 7 na safe tafara bude idanuwanta ahankali tana motsawa, Nauyi idanuwan sukai mata dan haka ta maidasu ta rufe kafin ta sake budewa tana motsawa ahankali ta tashi zaune tana duba gefenta taga bataga saleem dinba, Bude idanuwanta tayi sosai tana duba dakin taga bata gansa ba, Miqewa tsaye tai jiri dibarta ya zubar qasa, Bata damuba ta sake dafawa ta miqe tana nufar kofar ta bude tareda fitowa tana waiwayan koina, Waje gabaki daya ta fita tana dafe kirjinta ahankali dayayi nauyi ta tabbatarda dai Saleem ya tafi kenan... Faduwa tayi kofar gidan zaune tana cusa kanta cikin kafafunta kirjinta na zafi da nauyi kuka ya kasa zuwa kwata kwata. Tana gurin har rana ta fito sosai ta kasa motsawa sai daga baya ta iya daddafawa ta koma ciki ta zauna gaban kudin daya bar mata ta zuba musu ido batareda ko kyaftawa ba. A ranar kasa zuwa headquarters tayi sbd zazzabi me karfin gaske tareda ciwon zuciya dayake neman taso mata. Sai washe gari ta shirya kamar almajira ta nufi headquarters gurin ganinsu dad wanda daqyar aka bari ta gansu. Ganin yanayinsu ya sakata fita ta siyo musu bread da lemu da pure water ta kawo musu daqyar aka bari suka ci Sunaci tana kallansu tana hawaye masu dumi batareda sun cewa juna komaiba musamman dad da baya gani sosai. A haka ta wuni can sai dare ta dawo tai sallah ta kwanta shiru ba motsin komai. Sati guda tayi tana yawo gurinsu dad kafin aka fara shiga kotu dasu inda lamarin ya dauki zafi sosai basuda lawyer basuda me tsaya musu hakama itama dukkanin abinda take dashi a yanzu ya qare tsaf ko sisi batada shi sai yawo da busashen baki. Dan haka ta maida hankali sosai gurin addua da fadawa Allah ya duba lamarinsu yaji qan ahalinta yayi musu mafita a wannan case din. ******* Tsananin kusanci da Kauna tareda shaquwar datake tsakanin Dr Nico da AZIZ LIMBA ne ya saka wannan karan dole ya tattar yabaro Italy ya dawo Germany sbd shine likitansu daya zama family hakama ya zama tamkar da a gurin mama tin ba yanxu ba daman. Shine ya fara tarewa a Germany kafin isowansu dan haka koda suka iso ya kwana biyu sosai a qasar. Dr Nico tin lokacin Jinyar AZIZ LIMBA a lokacin rasuwar Ummitah shine ya kasance wanda yafi kowa sanin girman depression da trauma din daya samu kansa aciki sbd shima Yanada kanwar da ita kadai garesa bai hada komai da itaba, Mum dinsu yar Africa ce yar asalin Ghana wadda bayan ta rabu da Dad dinsa ta koma qasarta ta ghana tai aure ta haifi qanwarsa wadda agurin haihuwarta ta rasu kuma tin daga lokacin kanwarsa ta dawo hannunsa, Sbd kanwarsa dad dinsa ya rabu dashi ya kuma amsa hakan dan haka shima dan gwagwarmaya ya tashi sbd kanwarsa wadda bata taba sanin ba uba dayane ya haifesuba sbd dad dinsa ya rasu shima daga baya kaman yanda itama nata ya dade da rasuwa, Ya taso vaida buri baida fata saina ingata rayuwar Nicki, Ya samu daukaka daci gaban rayuwa bayan hardships da dama, Nicki ta taso cikin tsananin gatan daya reneta a cikinsa, Bata san komaiba bayan jin dadi da gata da tsananin kauna daga yayanta wanda yake komai sbd ita, Tayi karamin karatunta a italy kafin daga baya ta tafi America cigaba da karatu, Acan ma rayuwar jin dadi da hutu takeyi tareda gata me yawa duk da bata tareda yayanta wanda itama da sunansa take amfani, Nicki ta taso da wani irin yanayi na idan tanason abu bata yadda ko kadan wani ya rabesa, Bata yadda duk abinda takeso wani ya samesa ko ya tabasa, Tin tana yarinya take da wannan halin wanda ya saka yayanta yaqi sosai akan hakan sbd kaman yana taba kwakwalwanta dan hakanne ya tsaya sosai akanta sedai kuma hakan ya riga ya zama a jininta da cikin kanta ne, Tanada wani irin kishi akan komai nata koda kuwa abin wasa ne harta girma, Aurensa biyu yana rabuwa da matan sbd Nicki wadda ta kasa iya rayuwa dasu, Sbd tsananin kasa yadda da kowa ya rabi abinda yake nata ko take so Nicki zata iya attempting kashe kanta batareda tinanin komaiba wanda wannan shine babbar matsala da dr Nico yake fuskanta a tasa rayuwar sbd Nicki, Asalin mahaifin Nicki musulmi ne dan haka tana girma Nico ya sakata a musulunci batareda cutatarwa ko qyama ba kuma itama ta zaba hakan sbd akwai son musuluncin a zuciyarta dan haka ta tashi dag Nicki sai ta koma AYSH NICKY NICOLAS, Aysh nicky tana karatun likitanci kamar yayanta kuma tana gap da kammalawa dan haka dawowan yayanta Germany ya sakata dawowa gida daya dashi tinda ta kusa kammalawa sai tana zuwane tayi kwanaki ta dawo gida gurinsa. ****Kwanan Limbas daya da sauka a Germany Dr Nico ya iso gidan sbd duba AZIZ wanda har lokacin bai warware yanda y kamata dan haka a lokacinda AZIZ LIMBA ya fito palon da dr nico din yake tareda mama da Aysh Nicki suna gaisawa da mama Kaman a mafarki Aysh Nicky ta dago idanuwanta masu haske ta sauke akan AZIZ LIMBA wanda baisan da ita ba kwata kwata a gurin tana jin hankalinta na zarewa ahankali ahankali yana barin jikinta tareda dukkanin abinda yake zuciyarta batareda ta dauke kallanta akansa ba. A daidai wannan lokacin ne shi kuka sayd kiran saleem zad ya shigo wayarsa da Saleem yaje gurin latif ya samu yana dauka babu abinda saleem din ya fara fada masa sai "Zan zama donor din da kuke nema akan zaku kashe case din zaadens su samu freedom dinsu su samu damar gina wata rayuwar me tsafta" Cak komai na jikin Sayd ya dena aiki yana shiga shock din jin zancen wanda yasan har abada AZIZ LIMBA bazai taba yadda karban rayuwar wani kai tsaye bawai donor din daya cancanta ba wanda yake na wainda sun riga sun mutu a gangar jiki ne hakama bazai taba iya karban Zuciyar saleem ya rabasa da duniyaba sbd raya tasa yar to amma kuma falaq na tsananin buqatar zuciyar...... Shiru yayi yana kasa cewa komai sbd abune da baima isa yajewa AZIZ dashiba amma kuma koma menene yana buqatan Saleem din a kusa dan haka kai tsaye ya saka latif yayiwa saleem din komai na tahowa Germany batareda sanin AZIZ ba amma shima kansa bazai taba iya taba zuciyar Saleem ba sbd raya tasa 'yar amma dai zaiso zuwansa din idan har zai zama donor din dayake fada din. ***************** Jannah kuwa yau daga kotu da aka fito tafiyar kafa takeyi me tsananin tsayi cikin rana harta iso inda wata qaramar kasuwa datake kamar tasha a cike mutane kala kala da baqi da wainda ba baqin ba. Neman guri tayi a nesa da hayaniya ta zauna ahankali tana rufe idanuwanta da sukai jajir ta budesu tana hadiye yawu maqoshinta daya bushe. Ruwa takeso batada kudin siya dan haka ta sake saka hannunta a cikin aljihun doguwar rigar dayake jikinta ta taba ko zata dace da canji tinda haka take tana mantawa da canji a jikinta sbd damuwa da rashin sabo da rayuwar. Nera hamsi ta samu wadda ta sakata sauke ajiyan zuciya da sauri tana miqewa ta isa gurin me ruwan pure water ta siyo guda daya 50 naira ta dawo ta zauna inda ta tashi ta fasa ruwan zata saka a bakinta wata mata datake tsananin son ruwan itama ta zauna gefenta tana jan numfashi daqyar bakinta a tsananin bushe idanuwanta sun qanqance. "UMMINAH ZAN RUWA NIMA" juyowa jannah tayi da wani irin yanayi na faduwar gaba sbd sautin muryan da haka kawai ya saka gabanta faduwa ta saukar da idanuwanta akan matar. Tsakiyar idanuwanta matar ta kalla itama idanuwan matar ne suka saka ruwan hannunta subucewa tana jin kallan matar na sake saka gabanta faduwa. Ganin numfashin matar na neman barin kirjinta yasaka daukan ruwan da sauri tayi kanta ta saka mata a baki tana tallafota jikinta. Shan ruwan matar tayi tana dafe cikinta dake tsananin ciwo kafin me sai amai sosai tafara yi a jikin jannah din wadda tsananin tausayinta ya sakata tsayawa kallanta. Tana gama aman jannah ta wanke mata fuskanta ta miqe zata tafiyarta matar ta saka hannunta daya ta riqe jannah din tana cewa "Umminah karki barni, Umminah" Dakatawa Jannah tayi tareda juyowa idaniwanta na cikowa da hawaye taji tana kasa tafiya tabarta sbd kaman yanda matar ke neman umminta itama Miminta take nema a wannan gararriyar rayuwar datake ita kadai dan haka ta durquso ahankali ta bude baki tace "Ba ummi bace" Riqeta matar tayi da karfi tana girgiza kai a wahalce sbd karfinta daya qare tace "Ummina,karki barni ummina, Ki kaini gurin hamma, Umminah karki barni har abada bazan dake barinki ba duk wuya" Hawaye ne suka gangaro daga idanuwan jannah din tanajin zuciyarta na tsananin karaya tanajin bazata iya barinta dan haka ta kamata suka miqe taja hannunta dik da dukkaninsu babu me karfi matar ta qanqame hannun jannah kamar zata maidata cikinta suka bar gurin batareda ma sun san ina suka dosa ba. #MAMUH ZAFAFA BIYAR KALBIM 500 mamuhgee A DUNIYATA 500 Huguma AJIYA A DUHU 500 Billyn Abdul KIRJIN ME HANKALI 500 Miss xoxo Pay at 0022419171 AccessBank Maryam sani gummi Shedan biya 09033181070 Or mtn vtu at 09032345899*_KALBIM_* _Mamuhgee_ 94 *SHOP WITH ME by RANO* 08030811300 Best children's clothing shop💯 https://chat.whatsapp.com/Gk4H76TlRgyAAWIWgx3Jo7 Kina neman in da zaki samun kayan yara classy kaya na yan gayu at a very affordable price? Ko kina son fara kasuwancin kayan yara amma baki da jarin da zaki saro kayan? Nesa ta zo kusa, kiyi joining community din nan muna saka kaya masu kyau available da inganci a farashi me sauki da zaki dauka ki tallata har ki samu naki kema. Burinmu shine kowacce mace ta samu sanaar da zata dogara da kanta. *********** Hanyar gida suka nufa Jannah na sake bude fuskan matar da kyau daga hijabin dayake rufe fuskanta sbd ko akwai wanda zai ganta daya santa ya tafi da ita gida sbd tana tsoron tafiya da mahaifiyar wasu gurinta azo ana nema karshema aga laifinta da daukanta. Tafiya suke sakeyi me tsayi matar na sake riqe hannun Jannah cikin nata sosai kamar itace karamar yarinya jannah kuma uwarta, Yanda take qanqame hannun jannah din cikeda tsananin kauna da kasa iya barinta ya saka jannah juyowa da jajayen idanuwanta ta kalleta tana jin inama hannun tata mahaifiyarne take riqe dashi a hakan da tabbas dukkanin quncinta da baqin cikinta ya yaye. Gap da magrib suka isa gidan zuwa lokacin dukkaninsu sun tsananin gajiya dan haka zaunawa jannah tayi a tsakiyar dakin bayan ta shiga toilet ta debo musu ruwa a fanfo tafara bawa matar wadda tasha sosai itama sha tai ta xauna tana hutawa ahankali kafafunta na wani irin radadin gajiya. Sallah akai har aka fito masallaci tukuna ta iya tashi ta nufi toilet ta shige tayo Alwala ta kama matar itama takaita toilet da taimakonta tayi komai suka fito tare suka tada sallah sai yazamana kamar itace take jagorantar matar sallah sbd yanda ta ringa binta. Suna gamawa abincin data bari na cin darenta kafin ta fita ta janyo ta ajiye musu a gabansu ta kama hannun matar ahankali ta saka mata a ciki tana bude baki Ahankali tace "Kici abinci" Zuba mata idanuwanta masu tsananin kama dana 'yayanta matar tai cikeda kaunar jannah din da batasan ta inda take kwararo mata ta bude baki da muryanta me bayyanarda batada cikakkiyar lafiyar kai tace "Umminah kici, Umma tace kici" Dagowa jannah tai da idanuwanta dake sauyawa sbd yanda tai maganar kaman Mimintata take taji kewar uwarta idanuwanta suka ciko da hawaye suna gangarowa ahankali. Hannuwan Umman rawa suka dauka ta dorasu akan fuskan jannah tana goge mata tana cewa "Umminah bata kuka" Tsananta gudu hawayen jannah sukai tana rife idanuwanta ahankali tana tana share mata hawayen hankalinta na tashi jikinta na rawa sosai. Rikicewa Umman ke neman yi kanta na juyewa wanda ya saka Jannah bude idanuwanta tana dago hannunta ahankali ta dora akan na Umman dayake kan fuskanta tanata goge mata hawayen ta bude baki Ahankali tace "Jannah ce,jannah ce ba ummi ba, Ummi bata nan........ Bata qarasa ba Umman tayi baya da sauri tana kama kanta da hannuwanta biyu tana buga sosai tana girgiza kai da karfi koina jikinta na rawa tana cewa "Umminah zata kaini gurin hamma, Idan ba Umminah bace ki kaini gurin hamma, Gurin hamma nakeson zuwa, Ina hamma Abdul dinmu nida Umminah, Hamma yana can yana fada kullum mun fita yawo, Ya hanamu yawo, Ki kaini gurin hamma na fada masa Umminah batanan..." Yanda take buga kanta da karfi tana ambatar koma waye hamman da ummin ya saka Jannah tasowa da sauri tayi kanta tana kokarin riqota ta ture Jannah din da karfin gaske wanda ya sakata buguwa da bango har saida goshinta ya fasa kadan ta rintse idanuwanta cikin tsananin azaba amma bata taba gurin ba sbd Umman ta fara jiwa kanta rauni sbd yanda take yakushin fuskanta tana kiran Hamman da tsananin so da kaunar datake saka jannah fara hawaye tana sake komawa kanta da sauri batai wata wata ba ta rungumeta sbd dukkaninsu suna cikin qunci daya ne na rashin mutane mafi soyuwa a rayuwarsu. Yanda ta rungumeta da karfi ya saka duk yanda umman take tureta tana dukanta amma bata saketaba har saida Umman ta fasa wani irin kuka me tsananin karfi da radadin dayake cin zuciya da ruhinta tsawon shekarun gararanbar neman Hammanta da umminta datake yi batareda cikakken hankalinta haryanxu ya dawo jikinta ba duk da kuma ba tuburan take haukarba, Tayi yawo states da dama gurin nemansu, Ta kasa tina komai na rayuwarta bayan Hamma Abdul dinsu itada Ummi, Ta kasa tina ita kanta wace, Ta kasa tina ita wace,daga ina ta fito, Ina ne gidansu, Inane garinsu, Tayi yawon gidajen abinci tana aiki amma daga lokacinda aka fahimci ba cikakken hankali ne da ita ba haukanta yi takeyi tana tashi korarta akeyi, Idan abin ya kwanta baka taba sanin tanada juyewan hankali lafiya kalau zata samu aiki amma da zarar angane shikenan zaa sallameta, A wani kauye tayi rayuwa me tsayi sosai inda maigarin kauyen ya aureta duk da batada hankalin shi dai tai masa ta kwanta masa yana kaunarta, Bai taba komai da ita sbd magani da aketa nemar mata tsawon shekaru har Allah ya dauki ransa yabar duniya bata warke ba dan haka yayansa da matansa suka koreta ta sake shiga duniya wanda duk tsawon wannan lokacin bata taba dena ambatar sunan 'yayantaba. Jannah sake qanqameta tayi tana jin nutsuwa itama ayau ta samu wanda ta runguma tana sauke hawayen samun sassaucin abinda yake cin rayuwarta na tsananin kadaici da qunci. Ahankali Umman tafara rage kukanta yanayin qasa tana ambatar sunan Ummi wanda ya saka jannah amsawa dole sbd bata damar dawowa hayyacinta har ta dena kukan tayi shiru a jikin Jannah wanda itama tayi shiru babu me motsi a cikinsu har akai ishai suna hakan. Ahankali jannah ta janye jikinta ta miqe ta kamata suka koma suka sake alwala suka dawo sukai sallah Suna idarwa abincin ta sake janyowa ta kama hannunta ta saka mata a cikin abincin suka fara ci Ahankali kowannensu jikinsa a sanyaye har suka gama. Tattara gurin jannah tai ta shiga toilet tayi wanka ko data fito Umman tai bacci daga inda take zaune cikin tsananin gajia da zazzabi. Cikin tausayi jannah ta gyara mata kwanciyarta kafin itama ta saka doguwarta har qasa ta bacci taxo ta kwanta gefenta suka rufe da abin rufa guda duk da ya musu kadan. Kaman yanda akace mutum rahama ne hakan ne ya faru ga jannah sbd ayau datake tareda da wani ba ita kadaiba kaman yanda ta saba bacci ta samu yau din ya dauketa har safe wanda rabonta da hakan ta manta. Da asuba sallah sukai suka sake kwantawa Umma ta ringa baccinta hankali kwance Jannah ta zuba mata idanuwanta ahankali tana kallan fuskanta kafin ta gangaro da idanuwanta akan hancinta da gurbin idonta datake samun Kammanin wanda yake maqale a zuciyarta a lungu ta boyesa boyo na har abada da bazata fidda ba kuma bazata farfado ba. Numfashi ta sauke ahankali wasu hawaye masu dumi na gangaro mata na Saleem da har abada bazata yafewa limbas ba idan suka raya tasu yar ta hanyar rabasa da tasa rayuwar. Meyasa saleem zai mata hakan? Meyasa ya zabi barinta a lokacinda tafi komai da kowa buqatarsa, Rashinsa ya sakata jin rashin tsoro da shakkar janyo matarda bata saniba a jikinta tana samun nutsuwa da ita, Rashinsa ne ya sakata takejin matar da batasaniba a cikin ranta harma da tinanin inama uwartace. Sauti kukanta yafara ta saka hannuwanta biyu tana rufe bakinta tana juya baya kirjinta na nauyi. Kukan kewan iyayenta tayi sosai tareda tsananin kewar uwa datake tsananin buqata har jikinta na rawa kirjinta ciwo yake mata sosai tana sake rufe bakinta da hannuwanta.... Ba tsammani taji saukan hannun Umma a bayanta tana shafa bayanta ahankali jikinta a sanyaye tana jin kukan jannar har cikin ranta ta bude baki a hankali tace "Ummah batason kina kuka, Ki dena kuka kinji Umminah" Bude idanuwa jannah tayi tana kasa kallanta sedai tana jin yanda take rarrashinta cikeda kulawa har cikin ranta dan haka ta dakata da kukan tana rufe idanuwanta daga kwancen suka sake shiru tsawon lokaci har suka dawo daidai kowannensu kafin jannah ta miqe ta duba abincin datake dashi bread da lipton da ruwan zafin heater ta toilet sukasha sukai wanka ita kadai ta sauya kaya a cikin kayanta da suka fara ganin rayuwa suma, Umma kuma sbd ba kaya hakanan ta maida mata dana jikinta ta kama hannunta suka fita. Gurin dubo su Dad sukaje sukai wunin banza baa bari suka gansu ba haka suka dawo. Koda suka dawo bread da lemu suka sake ci Umma ta bige da baccin wahala. Shiru jannah tai tana jin inama itace take samun irin wannan baccin. Da dare gurin me abincin data bada kudin masu yawa tintini karbowa kawai takeyi taje ta karbo musu abinci mama na biye da ita kafa da kafa kamar qaramar yarinya. Suna dawowa sukaci abincin suka koshi suna gamawa suka kwanta jannah ta jima zaune bacci bai dauketa ba sai daga baya. Washe gari haka suka sake fita yawon garari taje da Umman inda suka hadu dan neman wanda ya santa amma sam babu kowa sai cewa yakeyi batada hankali motar zuwa wani garin neman yayanta take nema. Haka suka dawo a gajiye suka kwanta, Hakan ta kuma faruwa washe gari yawon neman wanda ya san Umma ta ringa yi kwana biyu cikin wahala da azabar yunwa da rana amma sam babu wani haske zancen daya ne mahaukaciyace ake ce mata. Jin tayi a zuciyarsa Umman na samu wani matsayi da gurbin uwar datake tsananin nemarwa kanta, Idan mutane na kallan Umman mahaukaciya mara kowa da baa san inda ta fitoba ita a ido da zuciyarta kallo da matsayin uwar datake nema ne Allah ya jeho mata, Idan Umma batada kowa itama batada kowa zata riqeta a matsayin Uwa,abokiyar rayuwa kuma sabon ahalin da zata ginawa Zaadens, Shigowan Umma rayuwarta tamkar wata rahama ce Allah ya kawo mata sbd tsananin son da umman ke mata duk da bata yadda ba umminta bace hakama itama kallan Miminta take mata dan haka tai Alqawarin riqeta su bawa juna sabuwar rayuwa tamkar jini daya, Zata zamo Zaadens zata rayu a cikinsu su bata sunansu,zasu bata gurbin Miminsu da suka rasa da yardar Allah. Da wannan ta budewa Umma zuciyarta gabaki dayanta ta karbeta kaman yanda Umman tin ranar farko bata dena mata kallan kauna me karfi ba hakama kaman yanda take a baya komai Hamma ne ke musu suna biye dashi kaman yayansa a yanzu ma biye take da jannah sawu da sawu koina tana gudun ta sake bace mata wanda hakan ke sake kashe zuciyar jannah akan Umman. Kowace safiya idan suka samu abinda suka ci wanka sukeyi su fita hannun Umman na cikin na jannah riqe su bazama yawon zuwa gurin su Dad wanda aka fara sharia me karfi akansu. Duk zuwan da sukeyi Hannunta na riqe dana Umma wadda tausayinta da kaunarta ya cikasu sbd ta zamo mutum daya kacal da Jannah take samun sassaucin qunci sbd ita duk da Batada hankali basu damu da hakan ba suma kamar jannah kallan cikakkiyar mutum suke mata sbd kaunar datakewa jannah a bayyane take daga nata bangaren. Ammar ne kadai ya kasa dawowa daidai sbd rasuwar Mimi data kasa sakinsa dan itace tamkar uwar data haifesa a rayuwarsa. Yawan zuwan dasuke ahankali ahankali Ummah ta fahimci Masoyan Jannah ne suke xuwa gurinsu dan haka itama tafara sabo da zuwa garesu din. #MAMUH ZAFAFA BIYAR KALBIM 500 mamuhgee A DUNIYATA 500 Huguma AJIYA A DUHU 500 Billyn Abdul KIRJIN ME HANKALI 500 Miss xoxo Pay at 0022419171 AccessBank Maryam sani gummi Shedan biya 09033181070 Or mtn vtu at 09032345899*_KALBIM_* _Mamuhgee_ 95 *SHOP WITH ME by RANO* 08030811300 Best children's clothing shop💯 https://chat.whatsapp.com/Gk4H76TlRgyAAWIWgx3Jo7 Kina neman in da zaki samun kayan yara classy kaya na yan gayu at a very affordable price? Ko kina son fara kasuwancin kayan yara amma baki da jarin da zaki saro kayan? Nesa ta zo kusa, kiyi joining community din nan muna saka kaya masu kyau available da inganci a farashi me sauki da zaki dauka ki tallata har ki samu naki kema. Burinmu shine kowacce mace ta samu sanaar da zata dogara da kanta. ************* Ahankali rayuwa tafara tafiya wata irin shaquwa me karfi da kauna me tsafta da tsananin karfi ta shiga tsakanin Ummah da jannah wadda ta koma kaman Uwar data haifeta take jin Umman, Komai na rayuwar Umman itace takeyi mata shi a yanzu cikeda kulawa da tattali, Itace tsaftace mata gashinta da tsaftar jikinta tareda farcenta da komai nata, Batada karfin siya mata sitira da wasu abubuwan dan hakan a cikin gidan ta shiga ta samowa Umman Kayan Mimi kusan guda biyar wainda da sune rayuwar take tafiyar musu yanzu, Shigowan Umma rayuwar jannah ta samu sassaucin qunci da damuwar datake ciki sbd tanada me debe mata kewa, Umma duk da batada cikakkiyar hankali amma ba hauka takeyiba idan dai ba yanayinta yaso tashi bane idan taso ganin hammanta wanda babu sbd tini Jannah ta riga ta cika gurbin Ummi amma kwata kwata bata son ganin hawaye na fitowa daga idanuwan jannah ko kadan koda kuwa itace ta sakata hawayen sbd idan ciwonta ya tashi taso ganin hamma babu tasha yiwa jannah rauni wanda daga baya zata dawo tana kukan raunin jannah din, Wata sabuwar babin azabar ce ta bude a rayuwar jannah ta bangaren ciwon Umman sbd sosai take fita hayyacinta tayiwa jannah abinda da yawa jini ke fita a jikinta amma a hakan jannah taji ta gani ta zabi cigaba da kaunarta har ranta bazata taba iya rabuwa da itaba sbd hakan sbd idan Miminta ce ahakan bazata taba guduntaba hakama ta tabbatarda idan ma ummi ce ko hamman bazasu gujeta ba dan haka ta rungumeta a hakan bata taba gajiyawa ba. Ta bangaren shariarsu Dad sosai komai ya dauki zafi duk ranar shiga kotu suna zuwa itada Ummah, Ita kanta Ummah ta samu kanta a kaddarar da batada dadi ta qunci da tarin baqin cikin rayuwar da Zaadens suke ciki sbd ahankali ahankali quncin dasuke ciki ya shigeta itama kwata kwata ba walwala ba farin ciki sai kuka yunwa azaba da baqin cikin da babu ranar fitarsa amma duk da hakan bata taba jin zata iya barin jannah ba wadda a take kira da Ummijan sbd Jannah ta kasa yadda da Ummin ita kuma Umman ta kasa yadda da jannah kadai saita hada da ummin. Lokaci yafara tafiya sosai ahankali yanayin shariar ya fara sauya salo wanda yake farin ciki da baqin ciki tareda tashin hankali sbd samun nasarar su Dad na nufin Saleem Zad ya sadaukar da rayuwarsa ga limbas. Wannan tinanin ya saka jannah shiga firgici da sabuwar damuwa me tsananin gaske gashi sunfara kaiwa maqura a rashin komai, Abincinta da zai dade bata nemaba sbd yawan kudinta a gurin me abinci ya rage yawa ne sosai sbd yanzu ba ita kadai bace dan haka tafara zuwa aiki gurin me abincin data nuna mata zata dauketa aiki. Itada Ummah suke zuwa aikin wanke wanken kayan abincin da aikin su fere dankali da doya haka da wanke kayan miya dasu cabbage. Ajiye Ummah takeyi gefe ta hanata komai itace me aikin wanda idan suka wuni suka dawo da dare bata iya bacci sbd azabar ciwon jiki sai ahankali Ummah ta gane abinda yake hanata bacci dan haka kullum suka dawo zata kwantar da ita ta ringa mata tausa cikeda kulawa da kauna ahakan Jannah ke samun dan bacci ya dauketa Ummah xata zauna ta ringa kulawa da ita tana fita har safe tukuna ita kuma idan sukaje gurin aikin ta kwanta tai nata baccin da bata samu da dare ba Jannah na aiki. *******Ayau da zaa shiga tinda safe taje tai aikin da zatai sauran ta sanarwa Madam dinsu zuwanta kotu dan haka ba musu ta bata damar zuwa. Suna gamawa sharp sharp ta fito itada Ummah suka kama hanyar kotu tana jin kirjinta na wani irin nauyi hakama hannuwanta har wani rawa sukeyi. Ummah ce ta kalleta a natse taga yanda duk take fita hayyacinta sbd fargaba kaman koyaushe idan zasu shiga kotun haka take sbd tsananin tsoron koyaushe zaa iya cewa yau an yankewa ahalinta hukuncin kisa. Wannan tinanin kadai rabata da nutsuwarta yake yana sakata shiga mummunan yanayin datake neman zarewa. Ahankali Ummah ta kwantar mata da kanta a jikinta tana shafa bayanta ahankali tana cewa "Zamu dawo dasu gida, Zasu biyomu gida" Koyaushe Ummah ta fada mata hakan jin takeyi tana samun yar nutsuwa da qwarin gwiwa duk da abu ne me wuyar gaske amma bata dena fadawa Allah ba itada Ummah koyaushe Adduarsu kenan. Koda suka isa kotun guri sika nema kaman koyaushe suka zauna jiran isowan su Dad daga gidan yari kafin judges. Zaman kusan awa daya sukai kafin aka iso dasu Dad din kowannensu ba kyan gani musamman Ammar da gabaki daya ya fita hayyacinsa, Ya koma kamar me ciwon sida ya bushe ya qanjame ya koma kamar wanda aka ciro daga rami, Maheer komawa yayi kamar mahaukacin dayake cikin tsananin qazanta, Dad kuwa ganinsa kwata kwata sai ahankali har wannan lokacin gashi su Maheer sun fisa jikin kuruciyar jure azaba da wahala. Dr ken kuwa yana gap da rasa ransa gava daya sbd kafarsa dai ta rube taimakon gaggawa yake buqata idan ba hakan ba zai iya rasa ransa. Anny ma kwata kwata batada kyan gani gashi mahaifinta shima case din ya biyo ta kansa tinda duka akwaisa a ciki wanted ake nemansa ido rufe amma ya boye baasan wace qasar yake ba. Miqewa Jannah tayi tsaye itada Ummah suna kallansu Dad din cikeda kauna da kewansu dake kasheta kowace daqiqa. Zuba musu idanuwanta dake cikowa da hawaye tayi tana musu kallan dayake kasheta sbd yanayinsu abune dayake yankar zuciyarta. Matsowa tayi tanason ta kama hannun mahaifinta ko zai samu sassaucin abinda yakeji itama ta samu sassaucin quncin dayake cin ranta amma aka dakatar da ita ahankali ta ambaci sunansa sautin ya shiga kunnensa ya dago yana kallan inda take baya iya ganinta sosai amma dai ya zuba mata idanuwansa yanajin sanyi yana dan ratsa ransa da ruhinsa. Ammar ma kallanta yayi yana jin baqin cikin da radadin halin da suka sanyata, Maheer ne kadai ya iya bude bakinsa ya sakar mata wani murmushin wahala daya sakata sunkuyar da kanta tana tsiyayo hawaye masu zafi. Ciki suka isa suka zauna Ummah na gefenta riqe da hannunta cikin nata tana share mata hawaye kaman zata ciro ciwon da Jannah din ke ji ta dawo dashi kirjinta. Shariar yau itace wadda ake saka ran zaa yanke hukunci dan haka dukkaninsu kowa jikinsa yake a mace babu iya dago kai ya kalli dan uwansa jimami da ciwo me radadi ne yake cike kirjin kowannesu, Kowannensu halinda Jannah zata shiga a rashinsu ne yake cin ransu da kuma rashin sanin me zasuje su tarar a gaban ubangijinsu akan abinda suka aikata sbd sun riga sun saddakar ga hukuncin kisan da zai iya hawa kansu. Bayan gama gabatar da sauran jawabai da manyan lawyers sukai da duka abinda aka hada dana fili da wanda akai bayan fage kotun tayi tsit a lokacinda babban alkali yake gabatar da hukuncin karshe na case din. "Bisa bayanai da dukkanin shedu na fili dana rubuce tareda kundun bincike da tabbaci da komai akan case din kotu ta yankewa dukkanin likitoci da Nurse da sukai aikin hukuncin kisa ta hanyar rataya banda Dr Ammar Zad wanda dukkanin bayanai da likitocin da aka saka suka dubasa sun tabbatarda baida cikakkiyar lafiyar kwakwalwa maana baida hankali dan haka Dzad,Maheer zad da Ammar Zad Zasuyi zaman shekara Daya gidan yari tareda aikin wahala me tsanani na horo a gidan yarin hakama kotu ta karbe dukkanin abinda suka mallaka na koina dan biyan diya ga rayukan da aka salwantar da hanyarsu hakama har abada kotu ta soke lasisin karatun Ammar zad na likitanci harma da sauran...." Jannah da zuciyarta ta dena bugawa a farkon maganarsa ta yanke hukuncin kisa ga likitocin jin banda Ammar zubewa qasa tai tana fasa wani irin kuka mai tsananin gaske ma samun dawowan rayuwarta daidai sbd saura kadan ta rasa ranta daga wannan hukuncin wanda ya sumar da dukkaninsu su Dad din suma sbd jin hukuncin da suka dauka hadda Ammar wanda bazasu iyaba zasu gwammaci a rataye su su dukan. Jin badashi ba Maheer ya fasa wani irin kuka mai tsuma zuciya daya saka Dad rungume Ammar jikinsa na tsananin rawa take ma yaji zuciyarsa ta kasa daukan mummunan shock din da suka shiga na dan lokaci ya dafe kirjinsa jikinsa na neman sakewa daga na Ammar din wanda ya kwata kwata baima cikin hankalinsa shi. Rungume jannah Ummah tayi da sauri tana fasa kuka itama ganin yanda jannah ke kukan tsananin ciwon daya danne kirjinta wanda ta tabbatarda Saleem Zad yabarsu tinda aka yankewa Ahalinsu wannan hukuncin me sassaucin da sun tabbatarda akwai abinda akai. Kukan farin ciki da tsananin ciwon zuci ne takeyi lokaci daya tareda tinanin tayaya zata iya fadawa su Dad Sun rasa saleem shima wanda har abada bazai dawoba sun rasasa kaman Mimi. Anny kuwa yanke jiki tai ta fadi a gurin hakama dr ken wanda take yafara shure shure zuciyarsa na neman bugawa, Hakama dr Abraham a rana daya zaa ratayesu dashi da 'dansa acan tasu qasar suma wanda ahalinsu ke cikin tsananin tashin hankali mai girma. Ammar zuri yayi baima da abin fada ko yi sbd ba komai yake ganewa ba ko fahimta wasu lokutan. Tattarosu akai zaa fita kotun dasu jannah ta miqe da sauri har tana faduwa ta nufesu da gudu ta kamo hannun Dad dinta da ake riqe dashi baya iya tsayuwa sbd hawan jininsa da yayi mummunan tashi. Da hannuwanta biyu dake tsananin rawa ta sake qanqame hannuwansa da ake banbareta cikin wani irin kukan quncin daya gama rufeta da dabaibaye rayuwarta muryanta na rawa cikeda wani irin kukan daya saka Dad din fashewa da kuka shima tace "Dad Zan jira ranar fitowanku, Zan jira Dad, Dad duk tsanani duk wuya ku tina ina nan ina jiran fitowanku, Dad dan Allah ka daure duk wuya ka fito inanan ina jiranku" Kuka Dad din kawai yakeyi yana jin kaman kirjinsa bazai iya daukan kukanta da maganganunta ba dan shikam kila bazai fito ba sbd bayajin yanada wata shekara guda din a gaba sedai ko Su Maheer. Cireta akeyi anason rabasu tana tsananta kukanta tanajin kaman zuciyarta ce ake kokarin rabata da ita sbd a hukuncinsu babu ziyara daga nan har ranar fitowansu. Su kansu dukkaninsu kuka sukeyi sosai banda Ammar da kansa ya juye baya iya komai yana tsaye yana kallan Jannah dake shidewa tana jin kaman ranta ne zai bar jikinta. Ummah ma riqe jannah tayi sosai tana kuka tana janta jikinta tana dukan wainda suke kokarin banbare jannah din daga Dad dinta. Dukkanin masu tausayi da raunin zuciyar dake kotun sauda suka tausayawa jannah cikeda tsananin sanyin jiki wasu hadda kwalla. Saida aka gada da karfi da duka aka iya rabasu da ita ta zube qasa a gurin tana fasa kuka me tsananin radadi da ciwo tanajin zuciyarta na mutuwa. Ummah dake kukan itama rungume jannar da bata hayyacinta kwata kwTa tai tana share mata hawaye tana kiran sunanta. Tana kallo aka sakasu mota aka rufe aka tafi dasu tafiyar da sai bayan shekara guda zata sake ganinsu, Tafiyar da batasan ko zata sake haduwa dasuba sbd azaba me tsananin da zasu tarar a zaman gidan yari, Tafiyar da basusan cewa Saleem suka rasaba suka sameta. Motar na ficewa daga harabar kotun idanuwanta suka rufe ahankali ta some a jikin Ummah dukkaninsu jikinta na sakewa. Taimakawa Ummah akai aka fitar dasu kotun zuwa waje acan Ummah sbd kan ba daidaiba ta zauna tareda dora kan jannah din a kafafunta tana rarrashinta a tinaninta bacci takeyi. Har yamma suna gurin tukuna jannah ta farfado ko gani batayi sosai ta miqe daga jikin Umman tana jin zuciyarta na qafewa. Dafawa tai ta tashi tareda miqawa Ummah hannu ta bude baki Ahankali tace "Ummah muje" Kama hannunta Umman tayi da sauri ta miqe suka farawa takawa suka bar gurin. #MAMUH #NEW LIFE #BESTlove #MothersLove #JANNAH ZAD #FATIMA UMMA ZAD #The ZAADENS #The LIMBAS #BESTSTORY #HOTLOVE #HOTROMANCE #CRAZY LOVE #BESTLOVERS ZAFAFA BIYAR KALBIM 500 mamuhgee A DUNIYATA 500 Huguma AJIYA A DUHU 500 Billyn Abdul KIRJIN ME HANKALI 500 Miss xoxo Pay at 0022419171 AccessBank Maryam sani gummi Shedan biya 09033181070 Or mtn vtu at 09032345899*_KALBIM_* _Mamuhgee_ 96 *SHOP WITH ME by RANO* 08030811300 Best children's clothing shop💯 https://chat.whatsapp.com/Gk4H76TlRgyAAWIWgx3Jo7 Kina neman in da zaki samun kayan yara classy kaya na yan gayu at a very affordable price? Ko kina son fara kasuwancin kayan yara amma baki da jarin da zaki saro kayan? Nesa ta zo kusa, kiyi joining community din nan muna saka kaya masu kyau available da inganci a farashi me sauki da zaki dauka ki tallata har ki samu naki kema. Burinmu shine kowacce mace ta samu sanaar da zata dogara da kanta. ********* Tafiya sukai me dan tsayi kafin jannah ta tsayar musu da mota suka hau batareda ta iya cewa komaiba sbd jikinta gabaki daya dayake a mace zuciyarta na bushewa da baqin ciki da damuwa. Ummah data ga yanayin jannah din hannunta ta saka a cikin nata ta kama tana hadewa da nata cikeda kauna me tsafta da karfi tana jin kamar ta yaye duka kuka da damuwar dake damun jannah din ta dawo dashi kanta. A hanya aka ajiyesu suka qaraso da kafa sbd kwata kwata baa barin motocin haya na shiga anguwar, Suna isowa gida silalewa jannah tai ta zauna tareda rufe idanuwanta tana rafka wani irin tagumi da nisa a tinani. Ummah zama tai gefenta tareda tagumin tana zubawa jannah idanuwanta shiru. Lokaci mai tsayi suka dauka a hakan kafin jannah ta iya sauke ajiyar zuciya tareda miqewa tsaye ta nufi toilet tayo Alwala tazo suka tada sallah. Suna zaune a gurin akai ishai suka miqe sukai, Kwata kwata batajin yunwa damuwa da qunci sun cike mata cikin amma tasan umman na buqatan abinci dan haka miqewa tai jiki ba karfi suka fito tareda umman hannun Ummah na cikin nata suka fara tafiya tinaninta yayi nisa jefa kafarta kawai takeyi har suka isa gurin madam dinsu jannah ta karba abincin da suke karba suka zauna anan can bayan kitchen Umman taci ta koshi ta sakata cin dole itama suna gamawa suka fito suka koma gida. Suna dawowa gida Umma ta kwantar da jannah kan kafafunta tana mata fita tana cewa tayi bacci. Rufe idanuwanta tayi ahankali tana jin nutsuwa da sassaucin komai na ratsata, Kasancewan Ummah a rayuwarta ta sani rahama ce me girman gaske wadda take sake jinta har cikin ranta, A yanxu Ummah danginta,uwa kuma ubanta hakama abokiyar rayuwa. Cikin Amincin Allah bacci me nutsuwa ya dauke a hakan wanda bata taba tinanin samun bacci ba a yau din. Kwana Ummah tayi har asuba tana gadi da kulawa da jannah din wadda ta tashi cikeda wani irin tawakkali da karfin zuciyar rungumar kowace irin kaddara da Allah zai jarabceta dashi, Allah ya bawa Ahalinta damar sake wata rayuwar idan sunyi juriya da hakurin shekara guda dan haka zata jure zata karba zata jira lokacin kuma tanawa Allah godiyar wannan damar daya basu. Ajiyar zuciya ta sauke ahankali a lokacinda ta kalli time a jikin wayar taga karfe goma na safe kuma lokacinda kotu ta basu ta barin gidan karfe goma sha daya ne dan haka ta kalli yan kayan datake dasu har ita har Ummah iyakacinsu jaka daya. Juyawa tayi ahankali ta kalli jakarta dake rataye jikin bango wadda ta dauki lokaci bata ko kalla inda take ba sbd abinda yake cikinta abu ne da har abada bazata iya budewa ta kalla ba. Hannu ta miqa ahankali ta ciro jakar tareda saka hannunta ciki ta ciro takardar da Saleem yabar mata sbd tinanin zata iya buqatan hakan. Akan envelope din dayake ciki hannunta ya fara sauka wanda ya sakata rintse idanuwanta ahankali tana jin kamar wuta ce hannunta ya sauka akai. Janye hannunta tayi ahankali tareda lalubo takardar Saleem wadda take dauke da Sunan garin da batama san yaya zatai pronouncing nasa ba amma kuma rayuwa ayanxu can zata kaita a cikin mutanen da batasan yaya zasu karbeta, Bata sansuba basu santa ba rana tsaka zataje garesu tace itace jikar yar uwarsu data shafe shekaru da rasuwa kuma yayanta vasu nema danginta ba sai yanxu. Numfashi ta sauke idanuwanta na jajir amma koma me zata tarar a kauyen ta shirya zata dauka zata daure zata zauna ta jira fitowan iyayenta su taru su koma kauyen sbd acan Allah kuma yanzu ya zabar musu rayuwa. Tattara musu kayansu tayi a jaka ta rufe ta sake duba dukkanin tamardun ahalinta na karatu da id cards nasu da sauran duka takardunsu masu mahimmanci suna hannunta dan haka ta sake sakasu qasan jakarta kafin ta miqe tsaye tareda miqawa Ummah hannu wadda ta kama da sauri tana miqewa. Numfashi me dumi jannah ta sake saukewa tana jin kirjinta na mata wani irin nauyi rauninta na neman bayyana sbd rayuwa taza mata matakin karshe na fadawa wata rayuwar wadda batasan wane qalubale kuma zata tarar ba. Bude kofar dakin tai ahankali tareda juyowa ta kalli Ummah da idanuwanta da sukai jajir wani irin radadi mara faduwa ne yake cinta da zuciyarta ta bude baki Ahankali cikin tsananin sanyi tace "Ummah zaki bini?? Da sauri Ummah ta gyada kai tana sake qanqame hannunta cikeda kauna datake ji har ranta tace "Duk inda zaki tafi bazan taba barinki ba har abada, Bazan qara rabuwa dake ba, Muna tare ba rabuwa UMMIJAN" Wani numfashin ta sake saukewa tareda ficewa daga dakin Ummah na sake murmushi a fuskanta na kasancewanta da Umminta. Suna fitowa daidai gate din gidan motocin kotu da lawyers suna isowa tareda yan media anan aka karbi dukkanin takardun komai dayake rubuce aka tabbatarda duk abinda yake rubuce na kadararsu ansamu takardar mallakarsa a cikin takardun data bayar akai komai ta saka hannu da hannunta dake rawa a qasan signature dinsu Dad dayake jere a takardun wanda saida aka kai musu gidan yari suka saka hannun sun bada komai tas tukuna. Juyawa tayi tabar gurin batareda ta iya juyowaba tanaji anata daukan hoton da yar hayaniya amma bata dakata ba bare juyowa sukai tafiyarsu itada Ummah. Tafiya sukai kafin suka isa gurin madam wadda tasan da komai kuma ta amince ta sakasu a cikin ma'aikatanta masu kwana kafin su samu abin tafiya dashi. Daki ne me dan girma wanda yake store ne na ajiyar abinci anan masu aikinta biyu rak data yadda dasu suke kwana sai kuma su jannah din yanxu. Bata bari ciwon dayake ranta ya takureta ba aikinta data saba ta kama jiki a mace tana kokarin hana kanta mara godiar Allah daga sassaucin da suka samu na hakan. Wuni tayi aiki har saida aka rufe restaurant din da dare tukuna ta samu ta watsa ruwa taxo tayi sallan ishai ta kwanta a gurin wahalallen bacci mai hade da zazzabi yana dauketa. Ummah ce ta dawo kusa da ita ta rufe mata jikinta ahankali tana daukan abin fifita tana kore mata sauro da kuma dan zafin dake akwai cikeda kulawa tana dan danna mata kafafunta da hannuwanta data san sun gaji matiqa. Washe gari da karfin jikinta ta tashi tana rage damuwa a ranta ta zauna tana taya Ummah gyara farcenta kafin ta gama ta kalli Umman tace "Ummah kiyi baccinki idan zanje nayi aikina idan na gama saina hada miki ruwan wanka kada ki fito kiyi zamanki tinda kinga madam tace batason wanda ba ma'aikacinta ba na fitowa gurin ayyukan, Kinji Ummah? Gyada kai Umman tayi tana cewa "Idan kin gaji ki aje ki dawo ki hutawanki kinji" Wani murmushi da iyakacinsa bakinta ne ya kubce mata daya saka ramammiyar fuskanta kyau tace "Ummah zan huta amma ba yanzu ba insha Allah" Itama umman murmushi tai mata tana kallanta harta fice. Madam din data iso tafara zuwa ta gaida cikeda girmamawa kafin ta wuce gurin aikinta wanda tafara da wani uban tarin yankan cabbages da vegetables tukuna ta koma fere Dankali wanda kusan buhu guda ne aka zazzage. Saida tai kusan rabi tukuna aka basu abincin breakfast ta karba ta koma dakin da suke takaiwa Ummah suka zauna sukaci suna gamawa Ummah taqi xama ta biyota ta zauna gefenta tana kallan yanda take fama da aikin fere dankalin dan haka itama ta karba ta fara tayata daman ta iya tinda tayi aiki a gidajen abinci itama. Kaman wasa sai gashi Ummah ta ringa tayata aikin da har yanzu bata wani qwareba sbd bata saba ba. Sai yamma sosai suka samu saukin aikin suka koma aikin wanke wanke. Ana magrib suka samu kammala komai suka tafi wanka tafara kaiwa umman ruwa toilet tayi kafin itama tayi, Sallah sukai suna gamawa dukkaninsu a gurin bacci ya daukesu kamar matacci na wahala. Sai dare sosai Ummah ta farka ta rufe jannah din tana mata aikin korar sauro da fita tanaji tana gyangyadi ahaka dai suka ga asuba. Washe gari ma haka suka wuni a aikin wahalar baji ba gani ba hutu sai dare suka samu hutu, A hankali suka fara shude kwanaki a cikin gurin wanda babu komai sai aikin bauta da wahala, Tinda suka shiga basu taba fitowa ba sbd babu inda zasu idanma sun fito din, Ahankali Ummah ta shiga cikin aikin sosai sbd bata iya kallan jannah cikin wahalar datai mata yawa ita kadai, Da farko Jannah bata bari sai daga baya ganin Umman bata iya bari hakama ta fita iya komai sai ya zamana tare suke komai, Ita kanta madam din dataga Ummah na aiki sosai saita dan qara musu kadan akan abinda take bawa jannah duk da ba yawa. Duk yanda Jannah zatai ta hane a gane Ummah ba lafiyayya bace tana yi sbd batason kowa yayi mata kallan mara hankali ko makamancin hakan, Tana kulawa da Ummah sosai tana kiyaye dik abinda zai tayar da ciwonta, Bata wasa da lulurar umman ko kadan, Itama Umman ta nata bangaren duk dare bata iya bacci kwana takeyi kulawa da Jannah bata barin sauro ya cijeta shiyasa take kwana tana kulawa da tattalinta kamar qaramar yarinya. Sauran abokan aikinsu basu san Ummah ba asalin mahaifiyarta bace sbd kaunar da tattalin datake mata shiyasa suke dan respecting Umman kadan. Tin jikinsu bai saba da wahala da yanayin gurinba har suka saba jikinsu ya sabu da wahalar sbd suna cikin wata na biyu a gurin. Lokacin da suka shiga wata na uku a lokacin ne albashin da suka samu yakai abinda suke nema na tafiya gida dan haka Jannah taje ta sanar da madam tafiya zasuyi. Da farko kamar bazata barsu tafiya ba amma ganin yanda jannah din tai wata irin rama da duhu sosai ya saka tausayinta cikata sbd yarinyar tabbas tana buqatar hutu da kwanciyar hankali koda a kauye ne indai zata samu nutsuwa. Sallamarsu tayi ta tattara dan abinda zata basu ta basu sukai godia cikeda girmamawa suka hada kayansu akan washe gari zasu tafi. A daren jannah bata iya bacci ba sbd bawa kanta karfin zuciyar iyawa, Basuda komai, Basuda abinda zasu zaunar da kansu a birni sbd a zero suke yanzu abincin da zasuci ma basuda hanyarsa matiqar bata tafi kauyenba ta nema danginsu dad din ba ta samar masu mafakar da suna fitowa zasu je su fake su dora sabuwar rayuwa daga can ba to tabbas suna fitowa garari da wulaqanta zasuyi dan haka ta zabi komawa kauyen ta karbe dukkanin zafi da tsangwamar da zaayiwa su Dad din kafin fitowarsu ta yanda koda zasu zo ta gama gyara alaqarta da dangin bazasu tozartasu ba idan sukaxo. #MAMUH ZAFAFA BIYAR KALBIM 500 mamuhgee A DUNIYATA 500 Huguma AJIYA A DUHU 500 Billyn Abdul KIRJIN ME HANKALI 500 Miss xoxo Pay at 0022419171 AccessBank Maryam sani gummi Shedan biya 09033181070 Or mtn vtu at 09032345899*_KALBIM_* _Mamuhgee_ 97 *SHOP WITH ME by RANO* 08030811300 Best children's clothing shop💯 https://chat.whatsapp.com/Gk4H76TlRgyAAWIWgx3Jo7 Kina neman in da zaki samun kayan yara classy kaya na yan gayu at a very affordable price? Ko kina son fara kasuwancin kayan yara amma baki da jarin da zaki saro kayan? Nesa ta zo kusa, kiyi joining community din nan muna saka kaya masu kyau available da inganci a farashi me sauki da zaki dauka ki tallata har ki samu naki kema. Burinmu shine kowacce mace ta samu sanaar da zata dogara da kanta. ************* Da wannan ta tashi da sassafe suka shirya tin asuba sukai wanka sukaci abincin data samar musu tin dare koda karfe 7 na safe tayi sun fito bayan sunyi sallama da abokan Aikinsu. Mota suka tara suka shiga zuwa tasha, Takardar hannunta ta sake budewa tana  karanta sunan porthcrt da sunan wani kauyen dayake da nisa sosai a cikinsa wanda batama san ya zatai pronouncing nasa tareda sunan familyn Mahaifiyarsu Dad duka a jiki harma da sunanta ita kanta mahaifiyarsu dad din da hotonta danasu dad din. Ajiyar zuciya ta sake saukewa ahankali tana lumshe idanuwanta tareda maida takardar jakarta ta rufe. Suna isa tasha babu bata lokaci akai directing nasu ga motar da zasu shiga tareda biyan kudin komai suka shiga suka zauna daga ita har Umman jikinsu a mace. Basuyi zaman mintina Arbain ba motar ta cika aka rufe koina motar ta tashi ahankali ana musu Allah ya kiyaye suka fita ta lumshe idanuwanta ahankali tana kwantawa jikin Ummah wadda ta fara shafa bayanta ahankali itama tanajin kamar tinaninta zai dawo sbd damuwa da nauyin kirjine ya rufeta sedai bata iya cewa komaiba. Tafiya sukai sosai kafin suka fice daga abuja suka kama hanya dakyau. Tinda suka hau hanya bata bude idanuwanta ba har sukai tafiyarda ta dauki awanni tukuna ta bude idanuwanta da sukai jajir tana dagowa daga jikin Ummah datai shiru ta zubawa fuskan jannah din idanuwanta cikeda kulawa da tinanin da batama san tanayi ba. Kasa kallan Umman jannah tai sai kawai ta maida kanta ta sake kwantarwa jikinta tana godewa Allah daya kawo Ummah rayuwarta dan a yanzu batama fatan yan uwan umman su bullo takoina tana fatan Ummah ta zama tata har mutuwa. Tafiya me tsayin gaske sukai wadda takaisu ga isa dare sosai dan haka ko bayan isarsu a tasha suka kwana cikin baqin dake kwana tasha tinda asuba aka sakasu motar kauyen da zasu tafi me tsananin nisan gaske. Ummah kadai ta siyawa Abinci wanda itama umman bata wani iya cinsa ba sbd sun galabaita, Jannah jin hankalinta na tashi tsoro da fargaban abinda zata iya tararwa na ciketa dan haka tayi shiru a sanyaye tana kallan hanya. Sai yamma lis suka isa kauyen wanda aka ajiyesu a farkonsa, Drivern da kansa ya hadasu da yan gari tareda fada musu gidan da zaa kaisu. Kallansu mutane dake gurin keyi suna mamakinsu sbd ganin yanda dukkaninsu sukai laushi sosai sukai zuru zuru musamman Jannah da bata taba tafiyar mota me tsayi ba hakama a rayuwarta bata taba xuwa kauye ba batama san rayuwa a daji shine kauyenba sai yanxu data samu kanta a dajin Allah me nisan gaske. Tsoro da fargaba me tsananin gaske ke shigarta tanajin kaman bazata iyaba amma kuma sbd samarwa ahalinta mafakar rufin asiri dole ta iya. Tafiyar qasa suka fara a wahale cikin kishirwa da gajia amma hakanan suka daure suka ringa bin wanda aka hadasu dashi yana tafiyarsa ba gajiya ko kadan sbd sabo. Gap da magrib suka isa cikin garin qauyen wanda sai a lokacin suka ga mutane sosai da gidaje sosai kowa na harkan gabansa, Fulanin daji ne kaf kauyen wanda kana kallansu ba tambaya zakasan kusan kowa a garin bafulatani ne baqaqe da farare gasunan kowa harkan gabansa yake. Kallansu akeyi cikeda mamakinsu sbd ana ganinsu anga baqin da suka taho daga nesa. Wani gida me girma da sashe sashe suka nufa har kofar gidan matashin ya kallesu yace "Ga gidan nan ku shiga sai kuyi bayani" Dagowa jannah tayi ta kallesa da idanuwanta da bakinta daya bushe qayau ta budesa tace "Mun gode sosai Allah ya saka da alkhairi" Kallanta yayi ya washe bakinsa yana cewa "ba damuwa ai da ganinku na gida ne" Sallama ya kwada a cikin gidan yana ambatar sunan abokinsa Garba dayake gidan. Garban ne ya fito daman yana kusa zai fito kenan. Washe da baki ya fito yana kallan bellon kafin ya maida kallansa kansu jannah dake tsaye a rakube. Zuba mata idanuwansa yayi sosai yana kallanta cikeda mamaki kafin ya maida kallansa kan Ummah ya juyo gurin Bello cikin fulatanci yace "Daga ina? Su waye? Waye suke nema? Kallansu bellon yayi shima cikin fulatanci yace "Daga binni suke nan gidan suka taho ka shiga dasu ka kaisu gurin kawu Modibbo mana. Garba dayaji daga binni suke da sauri yana washe baki ya kallesu yana cewa "Barkanku da zuwa, Bismillanku" Juyawa yayi ciki dasu yana cewa bello ya jirasa. Suna shiga gidan jannah ta sake riqe hannun Umma suka nufi ciki har babbar tsakar gidan wanda kowa ya fito aka fara kallansu cikeda mamaki. Modibbo ne babba a gidan kuma me fada a ji kuma mafadaci dan haka kowa hanyar dakin Modibbon ya kalla Garba na wucewa dasu can yana sake musu sannu bakinsa a washe. Modibbo ne ya fito sanye da Babbar rigarsa datake zuba qamshin ajiya maana qamshim rima da wularsa da shape dinta yafi kama da kofin silver fari tas dashi. Yana ganinsu sake gyara zaman hularsa yayi yana kallan Ummah ita datake babbah sai yaga ta sauke kallanta qasa. Jannah ya maida kallansa kanta yana cewa "Garba su waye? Daga ina kuma? Sake washe baki garba yayi daidai nan kawu Isiya da kawu jibo suka iso suna kallansu jannah din dukansu baki a sake. Garba yace "Modibbo baqi ne daga birni nan gidan suka taho" Maida kallansa kansu yayi yace "To baqi barkanku da zuwa, Daga ina? Numfashi jannah ta sauke ahankali ta bude bakinta jikinta na mutuwa gabaki daya tace "Sunana Jannah Zadeen jikar Hajiya Zeenah Zadeen..... Tsit sukai gurin gabaki dayansu tareda kallan junansu cikeda mamaki a bayyane kafin Modibbo ya hade fuska yana cewa "Kikace jikar haj zeenah?? Yar Mahmoud ko Ahmed? Sake sunkuyar da kanta tayi ahankali ta bude baki tace " 'yar Ahmed" "Da wane shedan zan iya gane hakan?? Hannunta ta zira a jakarta ta ciro hoton kakarta dasu Dad ta miqa masa. Karba yayi su kawu isiya na sake matsawa da sauri duba hoton suma cikeda mamakin abinda ya kawota gurinsu. Zubawa hoton idanuwansu sukai suka kafawa yar uwarsu idanuwansu sbd da mahaifin daya haifesu su ukun da haj zeenah din uwa daya uba daya suke. Shiru sukai kafin Modibbo ya dago ya zuba mata idanuwansa yana karantar kamannin Mahmoud da Ahmed daya sani tin suna yara suka taso tare amma tinda mahaifinsu yayi kudi ya bar qasar dasu basu sake nemansu ba haryanxu. Cikin nutsuwa da sanyi yace "Ina su Mahmoud da Ahmed din suke?? Dago jajayen idanuwanta tayi ahankali kai tsaye ba kwana kwana sbd batada karfin tsayawa boye komai sbd so take su karbeta a yanda Allah ya maidasu tace "Daddy Mahmoud ya rasu,Mimi ta rasu, Dad da sauran yan uwana biyu suna gidan yari sai bayan shekara guda zasu fito" Da sauri dukkaninsu suka kalleta kawu isiya na cewa "Mahmoud ya rasu?? Kasa cewa komai tayi. Jin hakan ya saka Modibbo cewa a kaisu jannah din dakin Yakumbo su huta a basu abinci da nono me dumi su sha su huta da kyau tukuna ayi magana daga baya idan ta nutsu yanda ya kamata. Dakin yakumbo aka kaisu matan gidan da yara na musu sannu da zuwa cikeda mutuntawa da farin cikin ganin jikar zeenah ce yau a gidan. Kasa cin komai jannah tayi wanka tayi da ruwan sanyi a bandakin da baida rufi take sanyi da zazzabi suka rufeta. Daqyar yakumbo ta sakata shan sabuwar madara me dumi wadda ta dan taimaka mata amma sallah kawai tayi ta dunqule guri daya tana rawar sanyi idanuwanta na tsiyayo da hawaye masu dumi. Ummah ma taci abinci tayi wankan amma itama zazzabin ne ya kwantar da ita. Washe gari duk yanda ake tinanin ciwon yabar jannah kasa barinta yayi dan haka tsoro ya kama su Modibbo kawu isiya yace karta mutu su tattarata su sallemeta yakumba tace aa. Ummah ta warware ita dan haka tafara kulawa da jannah din wadda ta rafke lokaci daya ta sake komawa kalar tausayi. Satinta daya ana jinyarta anata maganin hausa kafin tafara warwarewa ta dawo daidai. Sai a lokacin hankalinsu kawu ya fara kwantawa harma suka zauna da ita ta fada musu komai sedai ta boye cewan da sanin iyayenta akai komai tadai sanar dasu zuciyar da aka kawo musu ashe ta kisa ce bata hanyar gaskia bane batareda saninsu ba wanda hakan ne ya saka rufesu shekara daya. Su kawu Modibbo dasu kawu isiya da kukansu da komai na tausayin yan uwansu wanda kukansu kadai ita jannah tsoro ma ya ringa bata sbd tamkar kukan yayan aljanun dare haka suka ringa matso hawayen suna darzar idanuwa kaman masu gasar kuka sbd ta gani idan su Dad din suka fito ta fada musu da waye da waye sukai kuka sbd su samu rabo me tsoka sbd basu yadda da kakaf komai aka kwace musu ba dan kamar bame yiyuwa bane dan haka zasu kula da ita kamar kwai har su Dad din su fito su samu suma su lasa arziki. Bangaren Asalin kakansu na gidan daya dade da mutuwa Modibbo yace samarin gidan su saka karfi suyi aikin qasa su gyara daki biyu ne da bandaki sai madafa a gyarawa su Dad din kafin su fito. Su Garba da fodio da Idris sune matasa samarin gidan masu ji da lokaci tini suka fara aikin kowa da abokinsa ake aikin sbd kowa da kudirinsa na shirin dawowan su Dad din rayuwa a cikinsu da santaleliyar buturiyar 'yarsu data zama tamkar bayyanar Zinariya a kauyen. A cikin gida kuwa kamar jannah bazata iya rayuwar kauyenba sai kuma tafara sabawa sbd kauna da kulawa datake samu tako ina a gidan harma da wajen gidan wanda ya saka mata farin jini. A cikin gidan akwai budurwa tsararta 'yar kawu isiya wadda mijinta ya rasu ta dawo gida da yarinyarta 'daya itace tafara zama abokiyar hirarta. Fatma itace tafara fita da ita garin da gurare daban daban tin tana tsoron mutane harta saba tana shiga cikinsu sosai, A gidan kowa ta kansa yakeyi dan haka tana ganin lokaci yafara ja ta fara koyan sanaar saqa da siyarwan da Fatma keyi itama tafara ita kuma Ummah tana taya matan su Kawu harkan nono da manshanun da sukeyi dan haka itada Ummah sai ya zamana suna dan samun abinda suke kulawa da kansu basu bari sun zamarwa kowa lalura me gajiya ba. Kaunar datake tsakaninta da Ummanta ya wuce dukkanin tinanin da mutanen gidan dana waje keyi akansu sbd Ummah babu abinda takeyi a rayuwarta yanzu bayan duk abinda zata kula ta tattala rayuwar Ummijan dinta, Duk aikin wahalar datakeyi a gidan sbd jannah ne hakama duk daren Allah kwana takeyi kulawa da jannah dinta harta saba bata iya bacci sauro bin jannah,bata iya bacci idan jannah na cikin damuwa bata iya komai saida jannah dinta. #MAMUH*_KALBIM_* _Mamuhgee_ 98 *SHOP WITH ME by RANO* 08030811300 Best children's clothing shop💯 https://chat.whatsapp.com/Gk4H76TlRgyAAWIWgx3Jo7 Kina neman in da zaki samun kayan yara classy kaya na yan gayu at a very affordable price? Ko kina son fara kasuwancin kayan yara amma baki da jarin da zaki saro kayan? Nesa ta zo kusa, kiyi joining community din nan muna saka kaya masu kyau available da inganci a farashi me sauki da zaki dauka ki tallata har ki samu naki kema. Burinmu shine kowacce mace ta samu sanaar da zata dogara da kanta. ********** A bangaren jannah a yanzu data samu kwanciyar hankali da nutsuwar datake jin babuta sai a kauye da babu tashin hankali sai rayuwar rufin asiri, Ummah ce hasken idaniyarta da zuciyarta,ummah ce karfinta,Ummah kuzarinta,duk abinda takeyi tana yinsa ne sbd Ummah dan haka a ranta takejin Ummah uwartace da bazata iya rabuwa da itaba har abada dan haka ma ta yanke shawaran hada ahali da Ummah daga ranar da Dad dinta ya fito. Angama gyara dakunan da zasu zauna dan haka itada Ummah suka fara komawa da Fatma wadda take takure a rabe dakin yadikkonta. ******lokaci yafara tafiya sosai sbd shekara ta kusa cikewa dan haka lissafin su kawu sai ninkuwa yakeyi shi kawu isiya har batan lissafin abubuwan da zaiyi yakeyi, Shikuwa Modibbo bature yakeda niyar binsu ya zama duk inda zasu kafarsu kafarsa shima. Su garba kuwa shirin sosai sukeyi na yanda zasu tarbi ahalinda zasu iya zama sirikansu dan kuwa dadi da wuya zasu tsaya bazaa bar kauyen da jannah ba sai waninsu ya aureta ko zaa tafi kasar wajen dasu suma. Rayuwa tayiwa jannah da Ummah daidai babu me damuwar komai a cikinsu saita kewan nasu idan ta taso musu, Ciwon Ummah yana dadewa bai tashiba idanma ya tashi jannah rungumeta takeyi duk dukan dazai mata bata iya saketa haka zata ringa hadiyewa cikim azaba harda rauni da komai bata iya rabuwa da ita har saita dena ta fara kuka shine zata rungumeta susha kukansu tare su gama batareda wani yasan halinda suke ciki ba. Jannah Zad kaman yanda rayuwarta ta sauya ita kanta ta sauya tako ina, Rama da quncin data fito a cikinsa ya tafi, Jikinta ya dawo daidai bame qiba ba ba kuma ramammiya ba, Halaye da dabiunta da yawa rayuwa ta sauya mata su, Kaman yanda komai nata ya sauya hatta sunanta ya sauya sbd a yanzu kaf garin ba jannah suka santa ba da sunan da Ummanta ke kiranta aka santa dashi wato UmmiJan, Rayuwa ta koyar da ita darasi, Rayuwa a cikin mutane daban daban ya koyar da ita abubuwa da dama na rayuwa tareda sanin meye rayuwar a yanzu. Ahalin Modibbo sun kaunace ta a lokacinda batada kowa batada komai, Sun karbeta hannu bibbbiyu batareda gudunta ba sbd iyayenta sun gujesu dan haka har cikin ranta a yanzu take kaunarsu sbd a yanzu ne ta gane me dangi da yawa suke nufi, A kauye suke suke rayuwa a cikin dajin da babu wuta babu ruwa amma a hakan tasamu nutsuwar da bata samu ba a can inda daular take dan haka take rokon Allah ya bawa ahalinta ikon iya rayuwar da zasu taho su tarar anan din. Babbar muguwar halin da gidan suke dashi shine tsananin son abin duniya wanda a tsakanin kawunnin nata bata san wanne yafi wanne kwadayi da son abin duniya ba. ********BAYAN SHEKARA GUDA Ayau itace ranar datafi kowace rana a rayuwar UMMIJAN sbd itace ranar da zata isa abuja dan haduwa da mutanen da sune rayuwarta sune rabin jikinta data rasa. Itada kawu Isiya da Modibbo ne suka shirya tin asuba suka shirya da Ummah da kudin da suke tarawa itada Ummanta na tarban su Dad da lalurar motarsu da komai dana abincin da zasu ringa ci har dan tsawon lokaci kafin su samu aikin yi a kauyen da zasu tallafi kansu. A mota kasa rintsawa tai duk tsananin baccin dayake son daukanta kasawa tayi haka ta zubawa hanya ido zuciyarta na wani irin harbawa hannuwanta rawa sukeyi saida Ummah ta damqe mata su tana kallanta itama kallanta takeyi tana jin kaunar Ummah na sake rufeta sbd Ayau Allah ya kawo karshen damuwarsu. Su kawu kuwa sai zare idanuwa sukeyi a mota da manyan rigunansu da sukai uban squeezing. Tafiya me tsayi da azaba sukai har zuwa porthcrt wanda daga can a ranar suka kamo hanyar abuja wadda suka kwana suna dukan hanya kowa zuciyarsa baa kwance ba. Koda suka iso abuja anfito asuba har gari yayi haske dan haka a tasha sukai sallah su kawu suka siya bread manya manya da lemu suka zauna suka sha suka koshi dayake suna fitowa binni dan haka basuda wani kauyenci sosai. Ummah ma tayi tayi jannah taci wani abin amma sam ta kasa sakawa cikinta komai harbawa zuciyarta keyi sosai tsoro takeji sosai da fargaba. Ummah ganin jannah ta kasa cin komai itama kasa cin komai tayi suka samu mota suka hau suka kama hanyar prison. Karfe goma motarsu ta tsaya a bakin gate din da ake tsayawa jira. Fitowa tayi kafafunta na kasa daukanta tayi baya zata zube Ummah tayi saurin tareta tana kallan idanuwanta da sukai jajir kamar zasu kone sbd harbawan da zuciyarta keyi numfashinta fara sarkewa yayi ta zubawa kofar fitowan idanuwanta kowace daqiqa numfashinta sake sarkewa yakeyi tana kallan time na agogon dayake gaban qatuwar kofar shiga akan idonta karfe goma sha daya ta buga wadda tai daidai da bude karamar kofar da akai Ammar ne yafara fitowa wanda taja wani irin numfashi tana yin baya ahankali kafin Maheer ya sako kai waje shima a natse fuskarsa cikeda qasumbar fuskar data sauya kammaninsa ya koma kamar uztaz...... Sake numfashim me karfi ta sake ja idanuwanta na cikowa da hawaye masu tsananin zafinda kafin su gangaro Dad dinta ya sako kai ya fito take ta fasa wani kukan daya sakasu dagowa suna kallanta ta tafi wani irin gudun gaske ta nufesa tin bata qarasoba ya bude hannayensu yana jin ayau dukkanin baqin cikinsa da quncinsa ya qare. Fadawa tayi kansa suka rungume juna da karfin gaske yana sama da ita a jikinsa yana ambatar sunayen Allah cikeda gode masa. Kasa sakin juna sukai tana wani irin kukan farin cikin dayake neman fasa kirjinta. Shima qanqameta yake sake yi yana ambatar sunanta hannuwansa har rawar farin ciki sukeyi kamar zuciyarsa zata bude sbd farin ciki. Sakinsa tayi ahankali ta fada kan Maheer wanda yake jin tsananin kaunarta me karfin yana shafa kanta yana cewa "Alhamdullilah ya Allah" Sakinsa tayi ta juya kan Ammar dake kallanta yana tsiyayo hawayen kewarta ta fada jikinsa shima tana rungumesa cikeda tsananin sabuwar kaunarsa da kewansu duka. Rungume junasu sukai su dukansu suna kuka kafin suka saki juna suna juyawa gurinsu kawu da Ummah dake tsaye suna kallansu. Zubawa juna idanuwansu sukai tsakanin Dad dasu kawu sbd sun gane junansu tsaf dan haka kunyarsu ce ya rufe Dad din. Barka da fitowa su kawu sukai musu cikeda kulawa kafin Ummah itama tai musu sannu da zuwa suka fada mota gabaki dayansu suka bar gurin hannun jannah na cikin na mahaifinta dayan hannun kuma yana cikin na Ummah da suka saba zama a hakan. Tasha aka mayar dasu sbd basuda gurin zuwa. Sallah sukai gabaki dayansu kawu ya siyo musu bread da panke da lemu sukaci suka koshi kowannensu farin ciki kamar zai fasa zuciyoyinsu musamman Ammar daya kasa dauke idanuwansa daga kan jannah dayake kamar ya hadiyeta ya bata rayuwar da babu wanda zai tana ganinta babu farin cikinsa kamar yanxu da babu auren kowa akanta AZIZ LIMBA yabar rayuwarsu har abada ba dawowa. A tashar suka kwana a zaune suna manne da juna tana tsakanin Ahalinta da Ummanta. Ana sallame sallar asuba motar da zasubi ta fara shirin dagawa Karfe 7 motar ta fice daga tashar ta kama hanyar zuwansu kauyen da basusan rayuwar da zasu tarar acanba wadda basu tana sanin yaya akeyinta. #MAMUH #BESTStory #BEST LOVE #NEW LIFE #KALBIM #BEST ROMANCE #AZIZ AY LIMBA #JANNAH ZAD #AYSH NICKY #AMMAR ZAD #FATIMA UMMAH ZAD #DZAD #END OF PART 1 ALHAMDULILLAH INA GODIA GA ALLAH DAYA NUNA MANA KARSHEN PART 1 WANDA ZAMU FARA PART 2 INSHA ALLAH BAYAN RAMADAN IDAN ALLAH YA NUNA MANA WANDA KUMA GABAKI DAYA LABARIN INSHA ALLAH YANA CIKIN PART 2 WANNAN DUKA SHIMFIDA NE, INA ROKONKU AKAN KADA KUCE KOMAI GAMEDA TAFIYATA HUTU TIN YANXU SBD WLH TALLAHI BANDA LAFIYA SOSAI DAUREWA KAWAI NAKEYI SO BANASON NA LALATA MANA LABARIN SBD HALINDA NAKE CIKI SHIYASA, KUYI MUN UXURI KUNSAN DUK ME RAI YANA TAREDA ZUWAN LALURAR CIWO, KODA BAN TAFI HUTUN BA YANXU DOLE ZANJE HUTUN AZUMI DAN HAKA KUYI HAKURI MU JIRA DAWOWAN HUTU INSHA ALLAH ZAMU TSIMA MU NISHADANTU MU ILAMANTU KUMA MU SAMU DUK ABINDA MUKESO A LABARIN WANDA YAKE TAFE DA ABUBUWA DA YAWA. NGD ALLAH YA NUNA MANA MUN DAWO HUTU LAFIYA AMIN. ALLAH YA SAKAWA KOWA DA ALKHAIRINSA NA BIBIYATA DA KUKAI.