[07/11 9:03 pm] ★~AMMEY LAYLERH🤫: *🦅 MIKIYA 🦅* _A wonderful world & Special anti terroRism squad_ ____________________ *MARYAM NASEER MIRRAH* ~AMMEY LAYLERH ✍️~ ✯ *~🌠 JAJIRTATTU WRITER'S ASS.... 💫~* BOOK Two…………………………񆬍✍ 1&2 ♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡ _012/09/2024_ ❤🔥 BISMILLAHIRRAHMANIRRAHIM # OF THE LAW # A TAITOR's # ROMANCE # BLOCKBUSTER # A SOLDIER's # Courage # Hop0 # Is Crime ❤️❤️❤️❤️❤️ A duk loƙacin da Allah ya ƙaddara wanzuwar hallitar ɗan adam a doran ƙasa, to kuwa tabbas ko ya ƙi ko ya so akwai waɗansu tarin Ƙaddarorin da suke yin jerin gwano a gangar jiki da kuma ruhin ko wanne bawa, Inuwa wata aba ce da Ubangiji ya ke ƙaddara wanzuwarta manne a jikin kowanne abu, walau mai rai ko akasin haka... A kodayaushe tana bibiye da mune matuƙar bawa zai zuba maganansa zai lura da haka. Kalmar ƙaddara! Kalma ce mai ɗauke da rassa biyu walau ƙaddara mai kyau ko kishiyarta. Ƙaddara abokiyar tagwaitakar inuwa ce domin bawa ba ya taɓa shallake ma tarin ƙaddarorinsa, Duk iya gudun ka duk iya saurinka baka isa kujema tarin ƙaddarar da ubangijin sammai ya ƙaddara maka ba, sanin haka ya sa na fahimci karin maganar Malam bahaushe ta _Tun ran gini tun ran zane_ ta zauna ɗaram kwatankwacin yadda ake ɗora ƙwarya a gurbinta. Yau gani a matsayin matar aure wacce zata ci gaba da amsar wannan sunan har zuwa numfashina na ƙarshe, tafiya me zurfi ce ta kaimu wata anguwar da bansan ko wacce anguwa bace domin zuwa loƙacin na shiga kukan gasken. Tsaiwar da motocin sukayi ne yasa na fashimci mun kawo gidan su salman kenan, dan kuwa bazan ƙira shi da gidana ba. Hajiya Umma ce ta dafa kafaɗuna tare da faɗin. "Ki fito da ƙafar dama tare da bismillah Maryama" Wasu hawayene masu ɗumi suka sake wanke min ido shikenan ta tabbata kenan wayyo allah rayuwa na faɗa a cikin raina ina jin wani raunin dake son ɓallowa daga can ƙasan ƙasan zuciyana. Fusgar hannuna da naji an yine ya sanya ni ambatar sunan Allah a saman laɓɓana. Muryar gwaggo naji tana ruwan masiyar wai zaman uban me nake da har yanzu bazan fito ba, ko dan naga mota me kyau shine na maƙale. Allah sarki ita motar ta dama domin ni a loƙacin kukan tausayin kaina da kaina nake yi, ta sabuwar rayuwar da ƙaddara ta sake buɗe min sabon babinta. Wannan kyakkyawar dattijuwar ta ɗazu itane ta ceceni daga masifar gwaggo ta hanyar kama hannuwana zuwa cikin nata tafin hannun. "let go to ur forever home by grate of god" Ta faɗa a loƙacin da take shiga dani mahaukacin ƙaton get ɗin gidansu salman..... Haka suka shiga dani kaina a lulluɓe ina share ruwan hawayen da yaƙi tsayamin har zuwa loƙacin, tun a farkon shigarmu gidan na fara jiyo ihun ɓaɓatun gwaggo nata yaba gidan. Kuma ni kaina shaidar hakance ko daga yanayin yadda gidan ya ɗau haske tare da wani abu me laushin tsiya da naji ƙafana suna nitsewa a cikinsa. Amma duk hakan baisa naji wani abu daban akan auren ba haryanxu illama kalaman Anne da sukemin yawo a tsakar kaina shin me kalamanta suke nufi? Shine kawai fassarar amsar da nake nema a haukace ido rufa. Tunanina ne ya tsaya a sadda muka kai ƙofar shiga palon gidan, wata sabuwa kenan domin tuni ɗakin ya hautsine da maganganu jama'a kowa na tofa albarkacin bakinsa game da gidan. A falon aka zaunar dani wai wurin kakar ango a karan farko kenan da na ɗan ji mamaki, dan nasan dai salman baya da kaka a shegen surutunsa ya taɓa faɗamin shi baima san kakarshinba sai a photo ya santa. (Mebi ta ɓangaren Maman shine) na faɗi a raina ina ƙarasa zaunawa abinda ya sake kullemin kai shine yadda matar da suka ƙira da kakar ango itama ta amshemu a mutunce cike da girmama naji suna gaisawa da hajiya umma. Hannuwana naji an kama hakan ya tilastamin ɗago kaina don ganin ko waye. Idan nace mucu saida brain nawa ta juya karkuce nayi ƙarya domin a fusge sai naga face ɗin kyakykyawaer farar dattijuwar yamin kama da face ɗin dana taɓa sani a rayuwata. Saidai na manta inane a kuma ina hakan yasani risinar da kaina ƙasa ina jan ijiyar zuciya. Ganin yadda itama ta kafeni da nata idon. Dafa kaina tayi fuskarta ƙawace da kyakykyawan murmushi ta furta "Masha Allah da wanzuwarki a cikin tsatsona Marayma" Daga nan ta shiga kwararomin adda'oi su kuwa sauran ƴan kawo amarya tuni sun bazu a cikin gidan da naji anacewa ba anan zan zauna ba. Kana kuma abu mafi ƙara ɗaure kaina shine yadda naji Wannan matar tana waya tana cewa gobe Insha Allah jet ɗinsu da wari zai tashi, nan na shiga tambayar zuciyana dama su salman ɗin ba ƴan nan cikin lagos bane?, to amma kuma duk wanda yasan Isa manu a garin na lagos ya sanshi, bisne tambayar nawa nayi a zuciyata don bana da mai bani Amsarta. Tunanina ya katsene loƙacin dasu Hajj Umma suka firfito zasu tafi zance suke yi a juye wanda nidai ban gane masa. Domin ji nayi suna mata sallama suna cewa allah ya saukemu lafiya, su maman Abdalla sai wani yatsine yatsinen fuska ake. Domin makusa suke nema tako ta ina amma sun rasa. shi ya sanya suke wani huhhura hanci sama domin ba haka sukaso ganin rayuwana ta gyaruba, saidai basu sani ba duk abinda zai faru bawa rubutaccene tun daga rabbi izzati. shine yake tsara mana duk wasu tarin ƙaddarorinmu tun kamin muzo duniyar. Tunani ya sake katsewa ne a karo na biyy loƙacin da Hajiya umma take faɗin. "To _FULANI_ mu zamu koma ubangiji Allah ya basu zaman lafiya Ku kuma Allah ya sauke ku lafiya ita kuma yasa gidan zamane" (Ba ameen ba) na amsa a zuciyata. "To Merrah mukam zamu tafi duk abinda aka tsinta a gidan aure ɗan haƙuri ne domin kowa da haka yasa ba, barin m aure irin naki da babu ango babu dangin ango, Sai aje ata haƙuri da zaman haƙuri" Muryan ummansu yaya Ibrahim ya doki ƙofofin kunnuwana, ban gama dawowaa daga suman wucin gadin dana tafi ba na kuma tsinkayar muryar Matar da ake ƙira da fulani tana mai bata amsa ta cewa. "Kwarai kuwa zaman aure ɗan haƙuri! Rashin ganin ango ko danginsa kuma karki damu wata rana zaki sani domin mutane masu daraja ba a arha ko a sauƙi ake samun ganjnsu ba! Amma karfa ya zame miki wani abin damuwa very soon zaki sanshi harma ki ganshi, domin shi kamar walƙiya yake yanzu nan ƙya ganshi yanzu nan ya ɓacema ganinki don haka ki kasance cikin shiri da tsammani domin Malam bahaushe yana cewa _TSAMMACI ABINDA BA BAKA TSAMMATA BA_ don haka ki riƙe kalmar daram aranki inba da magoya bayinki saisu tayaki riƙe kalmar" Kafaf palon kowa tsayawa yayi yana kallon wannan dattijuwar matar ciki kuwa harda ni, bazance kaina ya kulle ba domin dama a kullen ake saidai gabana daya shiga dukan tara tara bama uku ba. Na shiga uku ni merrah Auren nawa ne kuma yazo min haka ajuye tamkar amaryar buzuzu. Ɗaya bayan ɗaya suka ringa ficewa motoci na ɗibarsu suna mayar dasu. Inaji ina gani haka a gaban idona kowa dazan ƙira da nawa ya tafi ya barni a wannan juyayyan gidan. Babu dadewa da tafiyansu matar farko da taje ɗaukana ta kama hannuna tana me kaini wani ɗaki wai anan zan kwana, baki ɗaya jikinane ya sake mutuwa mayafina na zame bayan fitar tana me sake tunasar dani tafiyar sassafene a gabanmu goben. Toilet na faɗa domin inada buƙatar sake watsama jikina ruwa kodan zafin da aka haɗama kaina. Har wani hayaƙi² ne ke fita a kaina tsabar zafin daya ɗauka... A ƙalla na ɗauki Good 30 minutes a bathroom ɗin kafin na fito ɗaure da Alwalana kayan dana cire na mayar tunda ina da tabbacin banda ko tsinke a gidan. Amma ga mamakina kodana fito sai na tarar da wasu riga da wando na barci masu kauri tare da madarar shanu me zafi, (Ikon Allah baya ƙarewa) na faɗi a zuciyata domin kuwa shi nake ta gani sai gashin zabbin da suma aka ajje duk akan table ɗin dake gaban gadon. Saida nayi nafila tare da adda'oi masu ɗan tsayi kana na janyo plat na naman domin ba karya sammm bana wasa da cikina, tak na tafe cikina da gashin naman nan na kora da madarar shanun me dumi sosae. Adda'ar kwanciya barci nayi ina shirin kwanciya fulani ta shigo dana rike sunanta daram.Tambayana tayi babu abinda nake da bukata nabata amsa da babu kana taja min ɗakin tana me fita,Wata sabuwa kuma tana fita na rushe da wani sabon kukan na sabuwar rayuwar dana tsinci kaina wadda ƙaddara ta kawoni izuwa wani matakin na daban. A haka har bansan tsawon loƙacin dana ɗauka ina kukanba haka bacci yayi awon gaba dani fuska fall burbushin hawaye. ƙiran sallar farko a kunne na haka na yunƙura na tashi inda na tashi da wani zazzafan zazzaɓi da ciwon kai wanda nasan kukan jiyana ya haddasa min zazzaɓi da ciwon kan. A wahala nakai kaima bathroom na yo alwala da nafila na fara ina nan zaune har aka shiga sallah nima nabi sahu nayi. Kaɗan garin ya fara haske a kuma loƙacin saiga mutane biyun nan sun shigo suna zama gefe da gefen gadon. A ladabce na gaidasu suka amsani fuska sake har suna tambayar yadda na kwana. Da lafiya na basu amsa tea me zafi suka ce na sha yanzu jet ɗinmu zai tashi in zanyi tafiya inda ta hawa motace bana iya cin komi hakan yasa nace bana sha, sukace na daure ko kadan ne dai nasha hakan ya sanya sama sama nasha na ture cup ɗin muna fita a bedroom ɗin. Kasancewar babu ƙarfi a jikina hakan ya sanya tafiyane ya koma kamar jan ƙafa nake haka muka kai gaban jet ɗin da ko a mafarki ban taɓa zaton zan taɓa hawansu. Haka jirginmu yayi landing daga farfajiyar gidan muna lulawa tare da keta gajimare...... *SALMAN* A haukace yayi kan surry cikin yanayin fita a hayyaci baiyi duba da halinda take a ciki ba na sumewar da tayi. Cikin zafin zuciya da amsa amon murya ya furta. "I swear u don't die with out tell me what about my bride,nace miki ina matana take? ko saina yi gutsi² da sassan jikinki kafin ki buɗe baki kimin magana" "Babban kuskure mafi muni a rayuwarka da zakay shine hannunka ya taɓa min ƴa wllh salman" Yaji muryan mom surry ta faɗa daga ta bayansa. Wani irin juyowa yayi a matukar fusace yana watsa mata wani mugun kallo. Itama da nata kallon na kashiga uku ta bishi tana me nufar inda ƴar nata take yashe a some. " wllh wllh taku ɗaya kika fara momi saina sari fuskarki idan kin musu kuma kara ki gani" salman ya faɗi a dake yana saro wata ƴar karamar wuka a jikinsa, Ido momi ta shiga rarrabawa tanasan tijarar salman babu abinda bazai iya aikata mata ba tunda ya rantse domin dama idan ƴan haukan suka motsa masa baya shakkun kowa a gidan bare ita dama daya gama renawa duk kuwa da tana matsayin yayar uwarsa. Wayarsa da yayi ƙara itane ta ceci momi ta fice a sace da zuwan taje ta debo masa police's. Be ankara da ficewar tan ba tunda ya ga daddy'nsa ne me ƙiran. "Salman ina ka shiga ne tun ɗazu ina ƙiran wayarka ba ka ɗagawa? Ka san fa ba na son hakan ka barni a zaune tun dadewa ina dakon jiran zuwanka. "Daddy ka faɗamin dama kitimurmurar da kuka ƙullamin kenan na auramin wannan guntun turawan, shi yasa furr ka hanani zuwa ɗaukar amarya kace yanzu maza basa zuwa ɗaukar amarya? Ehhhhhhh " ya faɗi a matukar harzuke. "Innalillahi, daddy's boy me me me kake nufi ka fahimtar dani, wllh bana ganewa ma ka kulle kaina tell mee tell me maza daddy's boy" "Sauya min matar da kuka yi mana kuka ɗaura min Surayyan momi bilkisu wacce ta gama rabawa turawa jikinta" Zumbur babu shiri Isa manu ya miƙe wani irin gumi na keto masa, "Kai kai banason zancen banza wacce surayyar kuma? Ko so kake saina zundumo maka ashar da cikin wayar ne" "Ba wani fa zancen kare kai daddy kawai kana son raina min hankaline wllh idan baku nemomin duk inda Merrah take ba wllh² saina tada hankalin kowa a gidan" "Kai durun uwaka dan ubanka yo aini a baybai ka kifeni ka fito kamin filla filla yadda zanfi ganewa" ya karashe maganar yana faman safa da marwa shi kadai yasan tashin hankalin da yake ciki idan har da gaske salman din yake. "Allah yasa ba shawuwa kayi da yawa ba" Daddy ya faɗi kayan jikinsa na jikewa da zufa idan har ta tabbata ba'a ɗaurawa salman aure da yarinyar ba ta tabbata kenan wannan shegen yasan shirunsu akan shi kome?. Ya ayyana hakan a zuciyarsa yana jin zuciyarsa na kartar ƙirjinsa da yake jin zafin har a cikin jikinsa. "Kayi shiru kenan da haɗin bakin naka ta tabbata ko daddy" "Haba haba salman kasan dai bazan taɓa ma haka ba saidai inda da wannan munafukar uwar taka suka haɗa baki suka muna fincemu dagani har hakai wllh boy" Daddy yafaɗi "Koma dai miye gani nan zuwa gidan kuma karda ka yarda kowa ya fice a gidan nan wllh domin duk sena kone kowa da kowa na rantse da Allahn da yake busa min numfashi" Yana fadar hakan ga gimtse wayar tare da sunkutar surry ko nauyinta baiji yayi waje, fitar san kofar gidan kuma yayi daidai da loƙacin da motocin police suka faka motarsu mom surry biye a bayansu. "Yawwa yallaɓai gashi nan ma ka gani? Ka gani da idonka ko? Wllh mahaukacine haukarsa ce ta motsa dama sanyi ya fara shigowa ai, karya kashe min ƴata ku kama shi yallaɓai" momi ta fadi tana zaga ye police ɗin. A tsawace police ɗin ya furta.. "Your under arrest her" Wani mugun kallo ya watsama police ɗin yana faɗin. "Akan wanne dalili kenan?" ya fada a rene yana shirin shigar da surry da take a sanƙame cikin motar police biyu sukayi rammm da shi.a fusace ya juwo da niyar naushin fuskar police ɗin ko kafin yayi wani yunƙuri ɗaya daga cikinsu yayi hanzarin buga basa ɗan kulkensa a gwiwowinsa duka biyun, hakan ne ya tilas ta shi kaiwa sukunne yana sakin ƙarar azaba. Amma duk da haka sake ƙoƙarin tashi yake jefa sury a cikin motar yayi yana zaro wuƙarsa yana wani zazzara musu ido. "Na rantse da Allah duk wanda ya sake matsowa inda nake kafin nayi dalilin rasa aikinsa ni saina kassara rayuwarsa kafin nan, kunsan kuwa waye _SALMAN_ ba da iyaka sunan mahaifina kaɗai nake amfani ba nima kaina haɗarine" (Hatsari) wata inkiya wanda alamu ya gama bayyana shine ogansu yama ɗayan dake dab da salman inkiya ta wutsiyar ido. Karaf ya faki idon salman yana komawa ta bayanshi yana damkar hannuwansa wani cikinsu yayi saurin ɗaura masa onka nan suka jefashi bayan motarsu ita kuma mom sury taja motar salman din dake akwai car key nata ajiki. Haka suka wuce da salman ita kuma ta kama hanyar zuwa gidanta, domin ma ba zataje gidansu salman ɗin ba kuma ta rantse wllh ko sama da ƙasa zata hade babu wanda ya isa ya raba wannan auren ya ɗauru kenan har gaban abada, domin farin cikin tilon ƴarta shine fiye da komai data mallaka a duniyar... _MERRAH_ Ba wata tafiya me tsaho bace ta kawo mu garin kano har tsaƙiyar fadar jet ɗin mu ya sauƙe, Nan naga ikon allah yau ga merrah a gidan sarauta (kenan ɗansu suka auramin kome?) na raya a zuciyata ina mai bin bayan su fulani da kuyangai suka kewamu. wata Brai layn car ce da ɗauke mu zuwa ɓangaren Fulani uwargi ga me martaba suraj. Har bakin part ɗinta aka kaimu nan ma kewaye mu akai haka ta kama hannuna cikin nata muna tunkarar katon palon ta bayan passes passes da muka ringa wucewa. A kan wata lallausar kilisa aka zaunar dani cikin ƙanƙanin loƙaci aka cika gabana da kayan ciye² dasu fruit babu kalan da babu, kaɗan naci domin zuwa yanzun sosae jikina ya sake tsanani taurin kai irin nawa da kuma dauriya ya sanya na shanye hakan. Wani lafiyayyen room aka kaini akace nayi wanka na huta hakan kuwa akayi nayi wankane wata farar halp bubu ɗin cotton less aka ajje min tare da blue black ɗin Alkyabba sai su undears haka na shirya bayan shiryawana da kamar 50 minutes aka aiko wata jakadiya wai nazo ana son gani na. Haka na bita domin komi nawa a wannan loƙacin ya tsaya cakkk, kawai ganinan dai kamar wata butum butumi haka nake kallon komi da ido na kuma duk umarnin da aka gindayamin kamar ba merrah ɗin da kuka sani ba. A salin fadar me martaba sarki suraj sunusi shureim fulani tamin jagora, zuciyata in bada bugu babu abinda take min. Kallo ɗaya yamun ya saki murmushi yana faɗin "Masha Allah Fulani yarinyance kuwa ashe na canka daidai" Kaina na sunkuyar kasa dan ba karamin kwarjini yamin ba gaisa shi nayi a ladabce. Amsani yayi yana min ƴar sokana wai shiba surukuwana bane na dena jin kunyarsa. Nidai kaina ƙasa sai wasa da nake da yatsun hannu na. Umarnin tafiya ya bamu fulani ta kama hannuna muka fice bayan adda'ar daya rakani da ita. Suna fita ya sarki suraj ya saƙi wani ƙasaitaccen murmushi a fili yana faɗin. "mabuɗin ƙofofin hasken ta bayyana!" Wayarsa ya ɗauka daga kan tumtum ɗin gabansa. Kai tsaye wata lamba ya dannawa ƙira magana me ɗan tsayi sukayi da wanda yake wayar, bayan ya gama da wanda sukayi kai tsaye lambar da sunan *AK PRINCE* ya bayyan ya dokama ƙira. _KUWAIT_ *AK* Tafiya yakeyi ahankali kamar bazai taka ƙasa ba kaman kuma wanda ke tsoron ƙasan haka yake tafiya. kai tsaye babban sashen sa ya nufa. yana sanye cikin ƙananan kaya black T-shirt da Black jeans tunda yake tafiyar yake wuce dogaraye dake tsaye wanda suka shiga taitaiyinsu suna kuma shiga nutsuwansu,sai ma wani irin girmamawan da suke bashi Ko kallo basa isan shi sai wanda suke take may bayane kawai ke amsa duk wanda ya watso gaisuwarsa ga AK ɗin. A baƙin ƙofan suka tsaya ƙiƙam suna bama kofan tsaro. Ta babban ƙayataccen palonsa ya huce kai tsaye zuwa bedroom nasa, yasa hannunsa kenan da niyar tamfirin wayarsa ya shiga may vebrating dole yaja ya tsaya yana me ɗauka ganin me ƙiran ne ya sanya shi jann ɗan ƙaramin tsuma "mtsssss" kafin ya picking call in tare da manna wayar a kunnen sa. Shiru yayi yaƙi yay magana har saida daga cannn sarki suraj ya furta. "Gaga kana da lafiya?" kai tsaye ya tambayeshi cikin larabci. "Da bana da ay daba jini ba" ya furta yana hararan wayan domin bayason sharuɗan da wannan tsohon yake shimfiɗa masa kai tsaye kamar wani ubansa danya haifi Oummeyn'shi aiba shi ya haifa. "Ka shirya zuwa Nigeria ɗaukan matan dana ɗaura maka aure da ita" "Tunda ga ɗan banza ba mezai hana ka haɗata da matanka su cike huɗu kenan" "ABDOUL-MALEEK wannan ɗin umarni nane" sarki suraj ya faɗi a tsawace yana datse ƙiran... "Mtssssss kama gaji ka sakar musu yarinya uban me zanyi da mata" (Hhhhhhhhhhhh munga ALIEYO ma malam AK😊☺😁 wllh idan kazo kana mana kuka irin na O'o ko hmmmm ubanka zamuci yaseen) Ya faɗi yana me fasa shiga bedroom ɗin domin yana da buƙatar yasha iska. *NIGERIA* _Isa manu pov_ [07/11 9:07 pm] ★~AMMEY LAYLERH🤫: *🦅 MIKIYA 🦅* _A wonderful world & Special anti terroRism squad_ ____________________ *MARYAM NASEER MIRRAH* ~AMMEY LAYLERH ✍️~ ✯ *~🌠 JAJIRTATTU WRITER'S ASS.... 💫~* BOOK Two…………………………񆬍✍ 3&4 ♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡ # The Amazing # CHANGER # Destiny # Betray # HotLove # ROMANCE ❤🔥 BISMILLAHIRRAHMANIRRAHIM 💚💛💜❤❤❤📴🔥♥♥ Ahankali yake saƙƙowa daga ƙerarriyar matattakalar benen ƙafafuwan nan nasa fari karr kamar a lashe kai bakace ya taba taka ƙasa bama da kafafuwan nasa, Yayinda lallausan hannunsa me kama da atafa yake riƙe da wayoyinsa guda biyu, ɗaya kirar Samsung ɗayar ƙirar Iphone X Manne a kunnensa yana waya. A nutse ya gama saƙƙowa daga upstairs ɗin yayin da cikin sassarfa yake tafiya amma inka kallesa zakasha a hankali yake tafiyan. Cikin zafin nama se faman harmutsa gashin kansa yake wayan ya janye a kunnensa yana fesar da numfashi. Se faman zuba ƙamshin mayun perfumes ɗinsa masu tsananin tsada yake,yeah shi kansa yasan yana ƙaunar ƙamshi yana kuma kashe ƙudi kwarai a kan turaruka sekace mace. Samm baya ƙashin narka maƙudan kuɗaɗensa akan ƙamshi komi nashi luxury da luxury kawai ake magana. Ba kamar ɗazu ba yanzu wasu shegun hoodie riga da wando rugby guntaye gaba ɗaya black. Fuskansa sanye da black prada goggle saboda kai tsaye baya iya shiga rana bai rufe idanunsa ba. Jikin nan sai walainiyan ɗaukan idanu yake. Tunda ya fito compound na gidan tight security ɗin dake zagaye da harabar wurin suka wani irin kame tare da sara may, mutane biyun suka yi gaba wasu biyun na take musu baya kai tsaye gaban shegen manyan car's ɗin dake jibge wuri guda suka nufa. Wata kafurar Colombia land aka buɗe may ya shiga, wanda kafff masarautar babu me irinta domin iyaka kuɗin ta idan wani me ƙaramar kwakwalwar yaji takan iya juyewa a take tsaban tsadan motan. Arms ne ya shiga driver sit yaja yana me rufewa, manyan motoci sosae suke shirin fita dashi amma ya dakatar da hakan ta hanyar musu nuni dasu zauna baya da buƙata. Kai tsaye motor'n arms ya cilla hancin motar suna nufar git din farko, nan suka shiga ratsa get get na gidan harsukar harabar masarautar, saida tight security'n suka tabbatar da motor'nsu Ak yayi nisa sosae kana suka rufa baya tare da dogarai. Kai tsaye Arms _SHISHA BAR KUWAIT_ ya nufa. land cruiser prado ɗin dake bin bayan motan security'n ce ta faka daga gefen kwalta na shiga Bar ɗin. Zaid dayaga fitan AK ɗin shine ya biyo bayansu, A parking lot na bar ɗin arms ya faka motan ya ɗauki good 10 minutes kafin ya ziro fararen sawayensa zuwa kan tap bries na harabar wurin. Gaba ɗayansa ya fito yana me nufar cikin wurin inda ƙiɗeɗe ke tashi kai tsaye na yaran manyan ƙasan. Wurine keɓantacce daya kasance ba kowa da kowane ke zuwa ba domin wurin kansa ba kowane ya sani ba. Da sauri mahboob dake ƙoƙarin fitowa daga wani passes na daban ya koma da baya, wayansa ya zaro a aljihun wandon jikinsa kai tsaye Mahaifinsa Al-hussien ya dokama kira Ana daga wayan ya furta. "Da da yanzu nazo wuce ta shisha bar naga shigan Ɗaya a cikin biyun su ko AK ko ZAID domin bamuyi kusa ba bare na tantancensu rungume da budurwa" daga tacan banji mene aka ce may ba naga dai ya koma cikin inda ya fito. Ak kuwa ɓangaren daya kasance na musamman ne ya nufa arms da kansa ne ya masa odaring tsadaddun wine, wani farin balarabe da ya shigo ne ya matsa zuwa ga Ak ya fara saving nashi drinks. Ɗan ɓata fuska yayi yana karɓan drink a wine glass da saurayin ke bashi, a nutse ya fara sipping na wine ɗin yana jingina da jikin cought din room ɗin. ɗan rolling idanunsa kafin ya fara tafiya zuwa inda pot na shisha yake sabon pipe dake leda yabuɗe yasa sannan yakai bakinshi ya zuka kafin ya ɗagakai yawani feso hayakin ta hanci da bakinsa cikin wani ɗan iskan salo.... Yana zaune a inda yake har loƙacin kamar walƙiya haka yaga wulgin motocin Da da hussien ɗinsu kuma ya tabbatar ba alkhairi bane ya fito dashi. Da ɗan sauri ya fiddo wayansa "JES maza ki fito da kayan aiki ga wani amaxonties news a bar na gintika layout kuwait" Datse wayan yayi yana sakin wani ɗan iskan smile. Cikin abinda be wuce 50 mint ba saiga almurun motar'n jesra me ƙirar panti grow cruiser land sai Toyota avalon 2024 ɗin dake bayanta. Fitowa tayi cikin shigan baƙar doguwan riga kuwait abaya. Idonta toshe da baƙin shade hannuwanta cikin hand bazan, tayi rolling da vail na abayar sai nose mark ɗin dake faran fuskanta bayan shade ɗin data sanya. "Let's go" ya faɗi ba tare daya bari tayi magana ba da hannu yama gurds ɗin dake biye da ita dasu dakata. Acan ɓangaren su Al-hussein kuma bayan shigansu wajen suka ƙira mahboob ya fito daga maɓoyarsa nan suka shiga neman Ak wuri wuri amma babu shi babu dalilinsa, cirko cirko sukay suna meda kallon kallo tsakanin su alhussein sai wucin ɓacin rai yake fesarwa. "Ban san abinda yasa ma na biye maka ba bayan inada tabbacin har yanzu akwai burbushin allurar haukar data saura a kanka" ya faɗa yana jefa masa wani kallo me kama da irin gargaɗin nan. "Na rantse Da da naga shigowansa wurin nan kuma na tabbata yana a cikin park ɗin nan dole don baici ace yafita a wurin ba" "Kai rufe min baki shasha kafin na ɓarar dakwai kan ka amshin hukuncin dazai biyo baya" Ya faɗi yana juyowa da niyar barin wurin a fusace. Cakkk yaja ƙafa ya tsaya ganin ɗaya a cikin biyun yaran da suke da shegen kamanni na tashin hankali abu ɗaya ne yake banbancesu ta hanyar voice nasu. Sai kuma halayyarsu kai tsaye.... Wani mugun kallo ya jefama jesra dake riƙe da camera a hannunta kafin ya buɗe baƙi cikin hasaluwa sosae ya jefa tambayar... "Waye anan" Wani ɗan murmushi ta saki tana waigawa bayanta tare da furta "ka canka mana kaida ƴaƴanka idan harkai ka gaza ganesu toni taya zan iya ganesun" wani ɗan ƙafta mata ido Zaid yayi ita kuma ta saki murmushi tana juyo da nufin kallon Su Da da. Daidai loƙacin da mahboob ya kawo mata wani zazzafan mari. Baikai ga face nata ba ta baya yaji an damƙi tsintsiyar hannunsa farar fatar hannun yabi da kallo domin yanason tantance ko waye. (Abdoul-maleek) ya furta kai tsaye domin haskensa ba irin me ɗaukar idanun nan bane irin na zaid. Amma idan basa guri ɗaya duk iya lissafinka baka isa tantance da waye kake tare ba sai suna a tare ne hasken ɗaya ke rinjayar ɗaya. "Tabbas wannan wasan lissafi akai akwai maƙirƙiransa" ya faɗi a bayyane yana juyawa ga Ak ɗin baki ɗayansa. Ƙoƙarin cillar da hannun Ak ɗin yayi amma saidai ya gaza amma dake shima tantirin kansa ne gashi soldier hakan yasan ya a karo na biyu hurgar da hannun Ak ɗin. Juyawa ga mahaifinsa yayi tare da furta "Wannan tatsuniyar dole ƙirƙirarta akai don haka ge gida DA'DAH" "Me na tafi kuma na barka kai anan ai kwara kai kaje nina tsaya da sunanka ya ɓaci ƙara nawan ya ɓaci domin kaine sarki na gobe MAHBOOB AL-HUSSEIN EMAAR's" Wani kalan ɗan waro ido zaid da jesra sukai suna me bin ɗan uwan nasu da ido alamar tambaya? Kafaɗa ya ɗaga musu alaman shima me sani ba kafin ya fara taku. Cikin taku ɗaya biyu ana ukun Da'dah ya cafki kafaɗun Ak tare da juyo dashi gaba kallon ido cikin ido suka bi juna dashi kafin Ak ya janye kafaɗansa a nutse yana furfa. "Saidai bana haɗa hanya ko tafiyana da masu rufa ido ko masu face uku sabo da jinina tafashashshene a tafashe yake idan irinsu suna kusanta kansu gareni wannan tafasar da yake zai iya ƙonesu ya saɓule su harma da ƙonewa ƙurmus!" Ya faɗi Yana gin gaba "ka iya buga crikect? Lallai wannan ɗan wasane da yafi ko wanne ɗan wasa kwarewe, da kyau shikenan dai nima ina da wani tsari ni dakai zamu buga ɗan ƙaramin wasa" "Karo da karo shike kayo babbar ɓarna amma in ka shirye muje saidai ka sani kafin buga wasan saika fara tabbatar da ingancin ƙasusuwan bayanka masu zame maka runfa! Dan ABDOUL-MALEEK AL-HASSAN EMAAR's ba kamar alawa bane da ko wanne kare ko doki zai iya lasa bane guguwane neeeeeee!!!" Wani irin shegen fito fifitttt zaid tare da Jesra suka saki a tare. "Hadari malafar duniya funkasau babban girki kaɗangaren bakin tulu a barka ka ɓata ruwa a kasheka ka fasa tulu. Kabewar kan kabari baƙin cikin me taushe murucin kan dutse kake baka fito ba saida ka shirya ABDOUL-MALEEK AL-HASSAN EMAAR's" Zaid ya jero masa duka uban kirarin nan jesra kuma ta shiga tafa masa. A wani irin mugun fusace Al-hussein (Da'dah) yabar wurin domin kwakwalwarsan na gab da gama rikicewa ta juyo idan ta juye kuma hauka ze musu kafin nan kuma dole yana son ganawa da MOH..... "Time is out" Kawai Ak ya faɗi yana barin haraban wurin yana komawa cikin bar ɗin. ★★★ _ALHUSSEN/ MOH_ Wani irin mugun mahaukacin gudu ya sanya akayi dasu hakan yasa cikin ƙanƙanin loƙaci suka isa EMAAR's. A haukace ya fito daga cikin motar duk irin yadda kuyangai da security ke bashi girma da miƙa gaisuwa baya ma ko jinsu duk kuwa da irin yadda yake ƙaunar a bashi girman. So kawai yake ya buɗe ido ya ganshi gaban MOH JIDDOH. Da balin ƙarfi ya daki door handle glass ɗin shiga part ɗin Moh jiddoh, tun daga wawakeken palonta ya shiga ƙiranta cikin sautu me amsa amo faɗi yake "Moh! Moh!! Moh!!!" Mo dake zaune ƙafa ɗaya kan ɗaya gabanta cike da fruit ta watso masa idonunta masu bashi tsoro wani sa'in saidai yau ba hakan a gabansa cikin hayagaga da cira sauti ya shiga furta... "Dole akwai gaskiyar abinda waɗan nan tantiran yaran suka sani MOH! Ki faɗamin gaskiya ki faɗa min gaskiya dole akwai abinda suka sani ko kuma sun gano ba kene _AINIHIN MAHAIFAYAR AL-HASSAN BA_ ko.......... Wani irin shirune ya gitta a wurin na wucin gadi sakamakon wani irin bahagon marin bayan hannun da Moh ta ɗauke fuskar Al-hhussein dashi... "Ban tabbatar da cewa kai cikakken mahaukaci bane sai yau Husseini! Ban san har yanzu allurar mahaukata na kan aikintaba akan kaba sai yau tirrrr dame haihuwar daƙiƙin ɗa irin husseini ! Ka sani wannan ɗin wani shuɗaɗɗan lamarine wanda yake daida da kamar gawar da aka haƙa rami aka bisne, idan kaga hakan ya bayyana wa duniya to kuwa tabbas gawar da aka haƙa rami aka bisne a ciki ƙabarinta ma za tayi magana! Ka sani wannan maganar shekaru 75 ake koshi uban nasu bazai taɓa sanin hakan ba bare zararrun ƴaƴansa haihuwar jiya da giya ta gama illata min rayuwarsu, bare kuma mahaukaciyar kakarsu da kullum take cikin tsananin hauka wacce a haka mutuwarta zata risketa a cikin haukan da ba ranar warkewarsa" "Da gaske nake Moh ke baki gaalamun hakan tattare da yaran ba kuma da kikecewa haka yau shekararki nawa da zuwa dubo _JADDERN ASHAAN_ ɗin. Shima ya faɗi cikin haƙiƙanin gaskiya da gaskiyarsa. Wani marin moh ta sake ɗauke fuskar Da'dah dashi. "Shekaru ubanka nace shekaru ubanka daya mutu zuciyarsa a kumbure, Ka sani _JADDERN ASHAAN_ tana ƙarƙashin kulawanane babu mahaluƙin daya isa zuwa inda take saini koda kuwa aljanine duk hatsabibancinsa duk iya tuggunsa. Matar da take ƙarƙashin ginin merlupin wanda kafff masarautar nan idan aka ɗaukeni sai kuwa ita mahaukaciyar sai mataccen ubanku iyaka mu kaɗaine muka san dashi, ko kai ban yarda na nuna maka sabo da allurar mahaukatanka kan motsawa time to time don haka idon't care your time to be" Fuuuuuuuuuu ta wuce ta barshi a wurin da rikon fuska. Zaune yake yana wani irin fesar da numfashin da yaji yana barazana wa rayuwarsa. Zubar daya gama wankemar jiki na ɗigowa daga saman fuskansa zuwa tafukan hannuwansa da suke a buɗe........ ★★★ ❤❤❤❤❤ _NIGERIA'N_ *KANO* A fusace Sarki suraj sunusu shureim ya shiga ɗakin fulani. Fulani dake kishingiɗe kan Royal chiar idanunta lumshe tana sauraran karatun alqur'ani na _AFIF MUHD TAJ_ ta buɗe idonta tana saukewa akan mijinta. Cikin tsantsan fushi da zallar fusatashin da AK yayi ya furta. "Lallai inason a shirya miƙa _ZAUJATIEY AL-MALEEK zuwa ƙasar mijinta a gobe goben nan! Tunda na fuskanci baya da sauran mutunci da kunya a idonsa harni ze dubi tsabar ido yace nime zai hana na haɗata a cikin nawa matan ta zama cikin ta huɗun! bazai gane babban gatan dana masa ba a yanzun sai zuwa gaba" Wani ƙasaitaccen murmushi fulani ta saki tana gyara zamanta cikin tattakonta ta furta "Ni yanzu miye nawa kaida Abdoul-maleek kuma ai ba'a shiga tsakanin faɗanku, wanda ya shiga kunya yake ji karka damu nima na matsu gaskiyar ta bayyana umarninka abin cikawatane Insha Allah marayme gobe a ƙasar kusa da garin mahaifiyarta zata kwana" Wani kallon kidai iya bakinki ya jefa mata yana fita a room ɗin baki ɗaya kwance ta koma tana maida idonta ta kulle. Kewa da ƙaunar Ƴarta na neman fasa mata ƙirji. So tabbas so take ƴar nata itama ta huta haka nan ta samu cikakken ƴanci ta gaji da ganinta ita ƴan jikokinta kowa daban daban ba a nutse ba so take komai yayi ya gama bayyana kansa. So take ƙaddarar data ratsa tsakani tazo ta gyara tsakanin ramin kura dana damisar haka nan. Gwani wajen iya farauta ya farauci kansa duk kuwa da cewar gwanancewa a yaƙi ba itace nasarar yaƙi ba gaskiyar mutum a kona ina itace nasararsa ita jarinsa. "Sol the promblem very soon Insha Allah" Ta furta tana jin nauyin da kirjinta ya mata na ɗan raguwa kaɗan. Tun a daren ita da kanta tashiga har ɓangaren da Merrah take wasu irin abubuwa ta bata harda na wanka dana turara jiki abubuwadai kala da kala haka ta ringa bata tare ta kwana da merrah ɗin wacce tace ma gobe za'a miƙata ƙasar mijinta. Nidai da ido kawai nake binta domin zuwa yanzu komi ga zama ba daidai ba a gareni daga nan sai nan can yana iya dole zanbi yadda alƙalamin ƙaddarata yake rubutamin daki daki har zuwa matakin da yake son kaini. Washe gari. Tun misalin goman safiyar ranar da yai daidai da talata kwana uku kenan da ɗaura min aure da zuwa yanzun nasan ba salman bane wanda shiba bansan waye mijin nawa ba. Wurin sauran matan sarkin ta rakani muka sake gaggaisawa duk da kuwa cewar mun gaisa dasu washe garin ranar da nazo, daga nan kai tsaye fada aka rakani wurin sarki suraj anan na ɗan jima sosae domin wasu dunkulallun kuramen maganganu daya ringa bani a baybay. Sha ɗaya da rabi na safe duk wanda ya kamata ya fito domin min rakiya ya hallara a compound na fadar. Bisa jagorancin ZAYD SURAJ SUNUSU SHUREIM da kuma jagorancin NAFISA WADA (Fulani) zamu tafi. Haka suka mana rakomu suna me binmu da fatan sauƙa lafiya, Sanyen nake cikin wani shegen almurun golding less. Me shegen tsada wanda kuɗaɗen da suka lasa suke a bayyane. Wata kafurar yellow'n Alkyabba me ratsin fari wacca aka ƙayawatata da brawn ɗin duwatsu ita kanta abar a kallace alkyabbar. ga nose mark ɗin da Fulani ta bani na sanya sai ɓakin glass ɗin dana toshe ido dashi ni kaɗai a raina sai mita nake (Wata sabuwa kenan ko duk wannan ɗin na miye?) Haka na shiya furtawa a raina har xuwa laƙacin da muka kai airpot a cikin wasu mayan ƙerarrun motoci na musamman ,A vip/section muka zauna loƙacin da muka shiga wani irin lumshe idanuna nayi kirjina namin wani irin lugudan da bansan ko na miye ba. Haka jirginmu ya keta hazo muna lulawa sararin samaniya wasu adda'oi na shiga karantawa a zuciyana ko zan samu abinda nake ji na lugudan da akemin a ƙirjina ko zai ragu, "Ya Salam" na furta a bayyane loƙacin da jirginmu ya gama daidaita a sararin samaniya tun ina iya lissafa loƙuta harna koma awanni daga haka har wani bacci yazo yayi awon gaba dani har bansan loƙacin da muka ɗauka ba. Sai idan loƙacin sallah yayi a tasheni nayi na sake komawa ga wani irin kaina da yake sara min kamar ya rabu da jikina. Sha biyun dare muka sauƙa a babban airpot ɗin kasar inda hasken streetling ya haskaka ko ina na harabar airpot ɗin wata dunkulallar farar mota ce tazo ɗaukar mu sai ɗaya kuma data kasance ta security ce. Da taimakon fulani na samu fitowa domin zuwa yanzu kaina kusan zan iyace muku ma a juye yake dan bana gane komi ga komi ɗin da nake gani bibbiyu. Ita ta shigar dani har cikin motar kafin kai tsaye mu lula cikin masarautar EMAAR's. Tafiya bame zurfi bace ta kawomu katon ginin masarautar wanda kallo ɗaya nama ginin kaina ya idasa rikicewa bawai na kyayun ginin ba sai kawai na yadda kaina ya sara da wani irin masifar ƙarfi ƙirjina ya wani irin buga. Take wani mayen zazzafan zzazzabi ya kawo min farmaki. Daidai da loƙacin da muke shiga ginin masarautar daidai wata iriyar Guguwar iska ce na turniƙe sararin samaniya masarautar ta shiga juyamin ilahirin compound ɗin yayi baƙiƙirin tamkar ruwan sama na daf da sauƙa. domin ba sautin da ke tashi sai gunjin fitar iska wanda guguwar ta ke kaɗawa da mugun ƙarfi gami da tashin duk abin da taci karo da shi zuwa sararin samaniya, abin mamaki har da ƙananun duwatsu iskan sama ta ke yi da su tamkar ledoji. ƙara gami da rugugi kawai ke tashi. A Kuma daidai wannan loƙacin MOH JIDDOH ta farka a firgice dafe da ƙirjinta dake barazana wa rayuwarta, wata irin zufa na wanko ilahirin jikinta ba ita kaɗai ba duk wani me alhaki akan haka haka ya tashi a furgicen haɗi da bugawar zuciya data ruhi. Wanj irinhaskene kuma ya gilma shuuuu tamkar ƙiftawar ido. Wani irin ƙasataccen murmushi fulani ta saki cike da nishaɗin ganin yarda al'amura suka soma haske tun a farkon tafiyar. Kallonta ta mayar kan merrah wacce kamar ma bata a cikin nutsuwarta. Gani tayi fatar jikinta yayi wani kalan hasken kyawu gami da jan hankalin duk wanda ya yi arba da arba dasu ga wani irin kwarjinin daya lulluɓe ta nan take. Shafo fuskanta tayi da hannun dama idanunta lumshe sumar idanunta na ɗigar da ruwan hawayen dake bin saman kuncinta. Kirari ta shiga jerama mahalicci tare da ambato a bayyane ta furta. "Ga Haske nan tafe a cikin masarautar EMAAR's me maganin duhu har abada zakara shi kaɗaine sarki. Masu rufaffun ido su farka haka nan game buɗaɗɗen na ainihin nan a gabanku! Makamin yaƙin ga bayyana!" To ai shikenan saimu gimtse haka nan ko?😊😁😀 # Shin me kalaman Waɗannan mutane suke nufi ne kam wai?# _SHIN WACECE JADDERN ASHAAN?_ _SHIN WACCE GASKIYAR BIYUNIN MAHAIFIN SU AK SUKE GUDUN SU AK ƊIN SU SANI?_ _SHIN MIYE HAƊIN MERRAH DA MASARAUTAR EMAAR's ?_ # Shin wanne kalan wasane za'a buga tsakanin AK da kuma Al-hussein (DA'DA)?# Duk ku biyo ni *AMMIEY LAYLERH* don warware muku zare da abawar dake cikin wannan littafi na *MIKIYA* Wanda koda kuɗinka saida rabonka Hajiya idan kin shirya jin kitumurmurar dake cikin wannan littafin saiki biyo *AMMEY LAYLERH* da ɗarinki biyar domin ayi tafiyar manya dake Hajjaju🙅🙌. Kibar tagumi😱 nibance kowa yayi tagumi tsakaninki da Allah idan har kinsan halin ɗari biyar ɗinne baki da to nayi haƙuri ki turim ɗarinki Huɗu nikuwa na antayaki *PAID GROUP* namu da muke posting kullum Insha Allah..... *Idan kin shirya saya saiki min magana a wannan number'n* 08104493215 *Idan kuma kai tsaye account naw kike da buƙatan shima ganan* 3206656358 Maryam Nasiru Fisrt Bank *Sayen na gari maida kuɗi gida koba haka ba😟😵😰 Dob Allah karmu ɓatama juna loƙaci idan baki shirya sayaba karkimin magana, Masu zagina harda ma masu kiran ai ance marubuciyar MIKIYA ta rasu ku sani Allah ne me kashewa da rayawa. Wata ma data tambayeni nace mata paid ne kai tsaye cewa tayi shikenan tama samu* _Kunsan dana tambayeta inda ta samu me tace min? Kai tsaye cemin tai a wurin ƙawarta, ni kuma sai nace mata saidai kuma banma fara rubutun part Two ɗin so dan allah a faɗi alkhairi ko ayi shiru😯_ [07/11 9:07 pm] ★~AMMEY LAYLERH🤫: *🦅 MIKIYA 🦅* _A wonderful world & Special anti terroRism squad_ ____________________ *MARYAM NASEER MIRRAH* ~AMMEY LAYLERH ✍️~ ✯ *~🌠 JAJIRTATTU WRITER'S ASS.... 💫~* BOOK Two…………………………񆬍✍ 5&6 ♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡ # The changer game's # Romance scene # His bloved_friend Meerah # His love towards ♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡ A daidai wannan loƙacin na'urorin dake jone da jikin me martaba sarki Hassan Al-hassan suka ɗauki wani irin kururuwar daya farkar da duk wani makusancin dake jikin ɓangarensa. AK shine mutum na farko daya fara bayyana ta cikin wata shegiyar ɓoyayyar hanyar da ko su Oum basu san da ita ba. Shigansa ɗakin daidai da gilmawar inuwar mutum ɗin da yayi wanda kai tsaye bazai tantance ko mace bane ko namiji. Wurin Paah ɗinsa ya nufa domin dama tunda ya dawo kasar baccin kirki bayayi, kullum yana cikin tsoron mahaifinsa da yake a tsakiyar damisai masu farautarsa. Hankali tashe yayi kan me martaba wanda daidai da shigowar shaƙiƙansa suma hankalin tashe. Kai tsaye hakan ke musu nuni da an sake _poisoning_ Sarki Hassan kenan? "La haula fi sha'atullah!" Shine kawai abinda OUM ta furta wani irin jiri na kwasarta. Da sauri zaid ya tare da tana faɗuwa a jikinsa zuciyarsa na wani irin mugun bugu. "Yau mun shiga Innalillah wa'inna ilaihir raji'un" Moh jiddoh ta faɗi tana yin kan me martaba, Wani mugun kallon da Ak ya watsa mata ne ya sanya ta jan birki jikinta ɗan rawa. RAZEERNERH (MAH) kuwa wani irin rumtse idanu tayi tare da cizar lips ɗinta da ƙasan hakorinta tanajin zuciyarta na mata bala'in bugun da tunda take bata taɓa jin irinsa ba sai akan mutum ɗaya. Kai tsaye Ak yama me martaba ɗaukar jarirai yana barin donpor room ɗin dashi, domin kai tsaye kulawan paah ɗinsa yake son yake son ta dawo hannunsa. "Kai jinin masu ɓakin jini ina zaka kaimin _ƊANA?_ bayan ga dr shazra ajaan nan na zuwa duba shi" "Daga yau na dakatar da duk wani likita dubamin mahaifina, a yanzun kulawansa yana ƙarƙashin iko nane kai tsaye idan kuma dame ja bismillah hanyar a buɗe take right?" Yana faɗar hakan ko inda suke bai sake kalla ba saida yakai hanyar fita kana murya a kausashe ya furta. "Ka biyoni da Habeebty _Ashaan Clinic resoom_ " Kai tsaye zaid daya san dashi yake ya rufa masa baya wannan ba loƙacin tashin hankali bane dan haka sauran jama'ar ɗakin suka rufa musu baya. ★★★ Da wani irin mugun speed yaja motar yana ficewa daga baki ɗaya passes ɗin mahaifinsa. Kai tsaye motar ambulance ɗin Masarautar ce ta ɗauki Oum A harabar building ɗin clinic ɗin Manyan Mercedes Benz black biyu na bayan ambulance ɗin ko kyakkyawan parking basuyiba sukai saurin fitowa Babu Wanda hankalinsa ba'a tashe ba sabo da tsananin tashin hankalin dake cikin zukatansu na ganin yadda AK ya shigada me martaba yayinda jigogin jikinsa suke jin rayuwarsu baya iya kwatanta rayuwa babushi ba, yayinda wasu ɓoyayyun zukatan suke jin Allah yasa nesace tazo kusa Ashshe ta gaida umma bi ma'ana ya mutu kenan. Mutuwar data kasance rigar kowa ko kayi fata ko karka fata dole dole dolen dole dole kasan zaka mutu kuma fa ita mutuwar nan ɗaya ce in akayita ba'a taɓa dawowa har gaban abada abadan, don me kuma zaka ma wanin ka fatan ya mutu. Arikice suka ƙaraso jikin ambulance ɗin da Oum ke ciki daidai loƙacin da nurses na cikin masarautar mata tareda doctors kusan biyar sukayo kan motar aka fito da ita. Cikin gaggawa akayi ciki da ita itama tun a hanya ake ɗaura mata ruwa dama tun acikin ambulance an ɗaura mata cannula tare da fara mata injections. Wani irin yarfar da hannuwansa zaid yayi yana jingina da jikin motan tare da kulle idonsa kansa na wani irin sara masa. Cikin wani irin tashin hankali likitoci da nurses ɗin asibitin suka rufa su Ak baya ganin Me martaba sarkinsu me adalci cikin wannan mummunan yanayin. Bayansu suke bi hankali tashe har zuwa cikin private aminity emergency suka shige, Da hannu yama sauran dactor's nuni da suje waje kafin cikin fusgar magana ya furta musu. "Oummuna! Habeebty itama tana da buƙatarku" Da kanshi ya shiga bama me martaba taimakon gaggawa bayan wasu dogon aune aune daya masa, wata iriyar ajiyar zuciya ya kawo a sadda me martaba ya kawo wani gauron numfashi. Su kuwa waje Wani irin kuka Razeenerh ke rusga tare da sauran mutane tuni wadda basa a wurin ma duk sun bayyana zuwa yanzun kuma. Wani irin rawa Jikin Adeenerh yake ganin yadda jikinta ke rawane ya sanya Jesra matse hannunta cikin nata hannun da ƙarfin daya sanya adeernerh ɗagowa. Jikinta ta faɗa tana me fashewa da wani irin cunkushashshen kukan da tun farko yaƙi zuwar mata... Dr Abaan Areef ne ya ƙaraso harabar inda duk suke tsaye babu wanda ya iya ko zama a cikinsu, kallon Razeenerh yayi sai kuma yaɗan saki ijiyan zuciya tare da faɗin. "Sorry ma'am you will have to wait hia and please calm your self insha Allah he'll be fine we'll do our all best just pray for him! And duk ku daina musu kuka Insha Allah komai Fine" Yana faɗin hakan Ya juya ya shige tareda wasu nurses biyu dasuka zo shigewa da gudu zuwa emagency room ɗin da oum take. Baya jesrah tayi cikin tsananin tashin hankali tareda fashewa da wani sabon kukan ganin yadda likitoci ke gudu suna shiga ɗakin Oum ɗinsu. uzaid dake gefenta ne yayi saurin tarota cikin qarfin hali ya buɗe bakinsa daƙyar shima yasamu iya furta mata. "Please Uktie just pray for him kinji and kiyi ta musu du'a kuka baya taɓa maganin damuwa okay?" Wani sabon kukan ta sake saki tareda rintse ido tana me furta. "Ya Allah ka bama Paah sauƙi tare da oum sauqi da sassaucin wannan masifa! Ya Allah ka zame musu bango majingina a cikin rayuwarsu Rabbi ka hana wani mahaluki damar sake taɓa mana paah ɗinmu! Innalillah Wa'innah ilaihir raji'un wannan ɗin wacce iriyar ƙaddarace Mai wuyar cinyewa..... Saurin rufe mata baki Mah ta yayi da sauri tana kallonta da idanuwanta dasuka kaɗa sukai jajir tsabar tashin hankalin da suke ciki ga wani mugun bugu da wani irin sanyin da taji yana ratsa mata har cikin jikinta. Juyawa tayi ahankali ta kalli gefenta daidai isowar Ak arikice ko gani sosai bayayi tsabar tashin hankali yana isowa ya tsaya cak tare dabin kowa na wurin da jajayen idonsa. Kallo ɗaya zaid yama Ak ya ɗauke kansa wani hawayen da besan sanda suka taruba sun cika jajayen idanuwansa shima nan take yaji gwiwowinsa sun gaza ɗaukarsa ya zube gaban ƙofar roon ɗin dake kusa dashi tareda rufe fuskarsa da tafukan hannayensa hawaye na tsinke masa masu zafi da ciwo... Ɗauke kansa yayi daga kallon zaid ɗin yayi ganin halinda da yashiga zuciyarsa na qara nauyi sosae. Har hawayen da yake ta ƙoƙarin dannewane na neman gangaro masa loƙacinda ya ɗago kansa ya ɗora idanuwansa kansu Mah tare da jesra da suma kukan suke, kallonsa ya mayar kan Adeenerh tana zaune gefen AYESHER tana ƙoƙarin kwantar mata da hankali. Al-hussien kuwa hannuwansa goye da bayansa sai kaiwa da komawa yake ya haɗa wata uban zuba. Moh jiddoh ma tsayen take hankalinta ba a kwance ba domin hankalinta ya rabu kashi biyu ne, neman hanyar da zata sadata da musassin abinda ya farun take, "Me hakan ke nufi?" Ta faɗi da tayi zaton a zuciyarta ne, Mahoob dake dab da itane ya furta. "Me kuwa hakan ke nufi bayan sake poisoning paah da akayi,moh nifa an fara sanja min tunani wllh yanzu zuciyata ta kasa zama wuri guda me waɗan nan jeron gwanon abubuwan suke nufi? Me yasa ake kullum cikin tryn na rayuwar paah ake? Me yasa duk sanda hakan ya faru Oum jesrah ke shiga comma itama?...... Tsawar da mahaifinsa ya buga masane ya sanya shi shanye sauran maganarsa ba tare da ya ida ba. Duk da ƙarancin shekarunta hakan besa ta gane mayucin halin da addarta deenerh take a ciki ba. Tsamm ta miƙe daga jikin mah kuma har yanzun bawai daina zubar hawayen tayi ba Hannuwan Adda deenerh ta riqo cikin nata tare da kwantar da kanta saman sholder na deenerh nan. ɗagowa ta sakeyi A Karo na biyu tana me sake riƙe dukkanin hannuwanta biyu tanata qoqarin ganin ta kwantar Mata da hankali cikin hawaye da tsananin tashin hankali ganin kamar ko bata a hayyacinta ne, Sabo da tunda abin yafaru ko motsin kirki batayiba bare hawaye saidai jajir da idanuwanta sukai Sam ita tafiso taganta tayi kuka yafi sauqi akan wannan halin dataga tashiga, Cikin muryan kuka jesh ta shiga faɗin. "Yi kuka! Kiyi kuka Adda deenerh paah ɗinmu ne fa baya da lafiya tare da oum, kinga duk nan kuka muke muma kalla ki gani! Kinga can gacan ma kalla _GARGALION'n_ ɗin Oum ma kukan yake hawaye yake zubarwa a karo na farko a rayuwasa tunda ya mallaki hankalin kansa..... Wani irin rumtse idk yayi yana barin wurin da sauri zuciyarsa na ƙoƙarin faso ƙirjinsa ta fito dole Anzo gaɓar da bazai sake be wani mahaluƙi damar sake taɓa may mahaifiba, Wasan yazo ƙarshe captering ɗin ya isa haka nan. Lumshe idanuwanta dasukai jajir tayi cikin tsananin tausayin _*Abdoul-maleek*_ Tabbas dukkaninsu suna cikin wani hali Amma shi ya fisu dan kuwa shu ƙunci da Sauyin rayuwa tuni ya daɗe da wargaza komai na cikin duniyarsa, ya tsallake yabar ƙasar sa. Yabar kowa nashi duk dan bama maƙiya ƙafa dan kuma ahalinsa su rayu cikin aminci tunda ta fashimci shi ɗin yafi tsole idanu. _AK_ Ahankali yake jujjuya ƙaramar kwalban dake gabansa wacce ajikinta aka rubuta Carbon Monoxide Poisoning da manyan baƙi, wacce yaci karo da ita a loƙacin da yake dab da barin ɗakin me marta ba. poison ne mafi matuƙar haɗari wanda kuskuren amfani dashi kan iya lalata sassan jikin mutum yayi damage nasa kai tsaye. Carbon monoxide poisoning itace poison ɗin da ayanzu samunta keda matuƙar wahala saboda haɗari da kuma illar da takeyiwa ɗan Adam kai tsaye. Ya tabbar da wannan cctv footage ɗin da yayi setting da na'urorin ɗakin ne ya toni asirin duk wanda yayi ƙoƙarin harar Mahaifin nasa. Murza kwalbar yaci gaba dayi ahankali fuskarsa ɗauke da wani irin ɓacin rai da fusatar da zuciyarsa. Hannunsa ɗaya dake ɗauke da cigarette ya kai bakinsa tare da zuƙan hayaƙin cigarette ɗin ya fesar cike da bacin rai, Kana ya ɗaura ƙafarsa ɗaya akan ɗaya haɗi da maida idanunsa ya lumshe. Wuta ne sosai keci azuciyarsa wutar da har yau ta kasa daina ruruwa. Amma saidai wayanda suka yi yunƙurin ciyar da paah ɗinsa poison ɗin ayanzu wutar ƙiyaayyar dake ci azuciyarsu tafi wanda ke ruruwa acikin tasa zuciyar ya sani, domin suma sun san sunyi kuskure tare da saɓanin lamba tunda harya suka bari ya farka kuwa. Ko so suke su ɓallo ma kansu hasalin haukarsa. Wanda zallar sarauta da isa da kuma uwa uba miskilancinsa suka bisne hakan. Lallai idan har suka bari allurarsu na sojoji ya motsa masa tabbas za'a ɓarin makauniya dole. Insha Allah daga rana me irin ta yau har gaban abada kenan da wani ze sake yunƙurin kashe mai mahaifi ba amma illar da sukeson yi mishi yafi su kasheshi muni ma. Haƙiƙa kowa damar shi yake nema a hannunsa shi kuma ya samu daman, saboda haka zaiyi amfani da loƙacinsa koda hakan na nufin rasa abubuwa nashi da dama, dole bazai ƙara saken da dahar zaa kuma yunƙurin cutar da paah ɗinsa ba ciki kuwa harda rayuwarsa. Hayaƙin cigarette ɗin ya saƙe zuƙa tare da buɗe rinannun idanunsa. "Its time for me to take revenge!!" Ya faɗa yana me miƙewa tsaye tare da juyawa ya fice daga cikin ɗakin. ♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡ _MADINAH_ *emirated place* shine kalmomin da wani babban majigin dake kusurwa kusurwa yake rubutawa yana kuma haska kowanne sashe na ciki place ɗin. Wani babban majigi ne na daban dake rubuce da manyan baƙin *Ash mayesh* Abinda ke rubuce kenan da manyan baƙi masu sheƙi da nuna haske a jikin wani katafaren signboard na karfe mai tsada. Wanda shi kansa signboard ɗin kallo ɗaya zaka masa kasan yaci kuɗi ...    Haɗaɗɗen gini ne irin na masarautun nan da sukayi zarra sukayi fice a cikin manyan masarautu. Yana yin tsarin ginin kuwa tsaf zaka ɗauka hotel ne ma saboda tsananin yadda yake da kyawu, da kuma passes daban daban dake cikin emirated ɗin wasu shegun benayene iyaka ganinka wanda aka tsarasu da iyaka zallar gilashi. Masarautar Madina kenan! Masarautace me cikakken iko wacce take taƙama da Al'adarta da kuma Addininta. Masarautar _Ash mayesh_ ginanniyar masarautace wacce take tsaye da ƙafafunta tun iyaye da kakanni, tun a wajen masarautar zaka fahimci ba ƙaramin Mutum ne ke mulkar Masarautar ta Ash mayesh ba cikin cikakken iko da kuma ginshira haɗi da wani irin kwarjinin daya ma duk wani family daya dangaci Ash mayesh ba. Bare kuma azo kan uwa uba me mulkartar baki ɗaya kaima me karatu ai kasan babu ƙarin bayani domin ɓatama kai loƙacine domin magana ake ta sarkin sarakan masarautun duniya. Wasu Arnayen Colombodia's car's ne suka shigo masarautar a tsiyace. Duka tarin motocin kalansu ɗayane domin a ka'idar masarautar basa fita da mota masu kaloli na samfurin banbancin company's. Bawai motacin ne babu ba A ahhh suna da tarin motocin na hauka ma kuwa wanda da za'a ba mutum iyaka wurin adana motocin cikin wannan masarautar me cike da ƙarfin iko kaɗai sai sun ishe ka har tattaɓa kunnenka rayuwa ba' a cikin talauci. Idan mutum ze fita ka'idar masarautar koda motoci hamsin zaka fita to dukka iri ɗaya zaka ɗauka in colombondia, in Bugatti, in Ralls R Rayce, in mercadex benz, in Toyota avalon, in jeep, in magarland, in Bcc, in Gtv, in Thailand, in colombian, kai duka dai ganan duk kalan da zaka fita dashi to zaka fitane da duka rakiyan wasu shegun tigh securitie's dogarai. A nan mahaukacin street house parking loot kawai na ada motoci suka faka. Tundaga kan sady pary, peery mian kowanne da sunan sa a wajen da motar da zasu faka daga rank ɗin jerin tagwayen sunan wuraren adana car's nasu yake. Mai karatu idan nace zan tsaya zayyano muku adadin kuɗi masu tarin yawa da aka kashe wajen zuba ado a departmen house kawai na adana motocin ma wanj sabon ɓatama kai loƙacinne sabo ma kuwa. Fari kall ɗin matashin da perry mian ɗin suka kewayena ta hanyar masa garkuwa. Matashi ne daya ɗan fara manyanta kaɗan wanda kuma na tabbar zallar hutu da kuma jin daɗine suka ɓoye manyan tan nashi. Cikin wani irin tafiyan ɗaukan hankali ya fara tafiya da zaratan sawayensa, perry mian ɗin nan jere a gaba da bayansa wasun su riƙe da wayoyinsa wasun su riƙe da systerm's nashi wasun su kuma ɗauke da lugage brifcase nashi. Tafiya yakeyi cikin tsananin gajiyawa da kuma cunkushewar da zuciyansa ya may tun ƙarshen wayan sa da ƙanwansan kuwa na safiyar ranan. Da sashen shi yayi niyan nufa amma kuma abinda yay masa tsai a kahon zuciyansa ya hana hakan tabbatuwa, dole ya nufi haromian Ash mayesh entrance na fadar mahaifinsa Sarki _ASHFUDDEERN MAYESH GAANTE's_ Tun daga harabar masarautar ya fara cin katari da manyan kuyangu, bayi, barori, ko wanne da kalan uniformɗinsu komai na masarautar tsare yake. Duka wasu nau'in ma'aaikatan dake compound na wurinne suka tsaya da duk abinda suke kawunansu ƙasa kasantuwar wanzuwar Babban ɗa ga sarki ash mayesh wato _Jalaludden Ash mayesh Gaante's_ Bayason hayaniya ko wacce irice kana bai fiye yawan magana ba shi yasa kwakwkwaran motsi ba'ayi idan yana da wanzuwarsa a wuri, hakan ya sanya ko irin busar algaitar nan baya da buƙata bare kirari. Mutum ne daya kasance me wani irin zafin zuciya wanda ya haddasa tsoronsa a zuciyar kowa. Saidai yana da tsananin tausayi zuciyarsa me raunice akan duk wani abu daya kasance rauninsa. Duk inda ya ratsa na'ura ce aikin buɗe masa hanya da rufewa bayan tayi kuruwar sanar da wanzuwarsa a wurin. Haka harya tsinci kansa a babbar fadar mahaifinsa me ƙarfin iko akan addinin musulincinsa. Wani farin dattijon balarabe ne ke gishin giɗe akan wata lafiyayyar Royal cough me tsananin laushi. Idanunsa sanye da wani yankakken farin gilashi na ƙara ƙarfin gani, jingine yake da cough ɗin Alqurani me girma riƙe a hannunsa gefen sa wata farar dattijuwa ce zaune hannunta riƙe da bowl ɗin dake ɗauke da yankakkun fruit tana ɗauka da slick tana sanha may a baki. Kansa ya sauƙe kas yana sakin ijiyar zuciya gabansa na mugun buga mai domin tsoron faɗan da yasan dole dolen dole yariskeshi ahar kullum indai zaiyi ido biyu da mahaifan nasa. Bisa bijerewa umarninsu da yayi na ƙin amsar sarautar da yayi shi kima alhalin ba laifinsa bane sun riga da sun sani, Wata shuɗaɗɗiyar ƙaddara ce data gimla ta cikin rayuwarsa shekaru masu dan dama wanda. Amma duk da hakan baya taɓa shallake faɗan Ash da kuma Queen Lajja ɗinsa. Ba tare da Ash mayesh ya duba inda yake ba ya furta. "Uhmmm meke tafe da isashshe kuma a wannan loƙacin?" Idonsa sam ba'a kansa yake ba yana a kan Al'Qur anin da yake dubawa. "Ya Abana DID........ Taryar numfashinsa mahaifin nashi yayi ta hanyar ɗaga masa hannu "Na sani DIDI tayi magana dani kai tsaye kuma nayi magana da zayeed ba buƙatar maimaicin hakan" Da hannun ya masa alama da yajekawai ɗan satar kallon Lajja yayi saidai ko ƙyallin idonta be samu gani ba jiki mace a sanyaye ya juya yana farin barin parlorun. Saida yaje daf da ƙofar fita ya tsinkayi nusassiyar muryantan me cije da zallar damuwa da rauni tana me faɗin. "Lil Anum Asha tazo inason ganin ta" Saurin juyawa yayi yana ɗauke kwallar daya tarun masa da zayeed Ash yakusa cin karo. Saurin taro ɗan uwansa yayi yana faɗin "Subhanallah jalaal Ash lafiyanka?" "Kaje kazo ma da Lajja lil Anum asha" "Asha anum? okay" Sakinsa yayi yana komawa da baya wani ɗan jiriri na shirin kwasar sa ya kayar. Jingina yayi da jikin glash yanajin sadda idanunsa ke cikowa da ruwan hawaye ya rasa ta yadda zaiyi yagaya kawo ƙarshen waɗan nan abubuwan da sukayi jerin gwanan wa rayuwarsa, Yana a yadda yake zayeed ya wuce da Lil Anum asha wacce kallo ɗaya tama Pappin nata ta ɗauke kanta tana me fuskantar gabanta. Fuskansa babu walwala ya bar wurin yana ɗaukar entrance ɗin da zaya sada shi da passes house ɗin ba tare daya nemi abin hawaba. Tafiya me ɗan nisa ne ya sada shi da sassan ginin gidansa me wani irin amintaccen kyawu. On tampring door handle ɗin yayi kana ya kutsa kansa da babban palon magamar gidan baki ɗaya. Oum Anum asha tana zaune hannunta ɗauke da Sultan meerah Jall. Da sallama a bakinsa ya shigo bayan ya cire cover shoe ɗin dake ƙafarsa sanyi da ƙamshin palon na shigarshi loƙaci guda. Da gudu irin nasu na yara nufo inda jalaal ash ɗin yake, ɗaukar yaron yayi yana mannashi da ƙirjinsa da yake buga masa, da hannu ya yafito Oum Asha kyakykyawar macece sosae. Fuskanta ɗauke da murmushinta mekyau ta ƙariso gabansa kwantar da gefen kafaɗarsa tayi tare da furta. "Komai na duniya dan haƙurine komai zai wuce kamar wani abu bai taɓa faruwa ba kaji Zauj" Kanta ya ɗan shafa zuwa fuskanta shima yana faɗin. "Bath first kafin dinner pls" Zare jikinta anashi tayi hanyar sama ta nufa don cika umarninsa. "Amma yau Asha Jikinta yayi sauƙi right?" kanta taɗan kaɗa may tana me ƙarasa hayewa saman, bata ɗauki woni dogon loƙaci ba ta fito tana me sanar ta gama haɗa mishi Sauƙe sultan meerah yayi ya nufi upsaid ɗin.... ★★★ Kowa besan da zuwansu ba har sai washe garin ranar domin kowa yana a cikin alhinine, kuma alhamdullih Oum ma ta farka saidai Ak yaƙi bayyanama kowa hakan me martaba kuwa dama tun a daren ya farka. Jesrah ce tama fulani jagora har zuwa ɗakin da Oum take ba tare da Merrah taje ba domin ita kanta jesrah ɗin bata san fulanin tare take da baƙuwa ba. Ta jima sosae tare da oum ɗin kana ta koma kodan merrah data baro ita kaɗai, shi kuwa zayd suraj yana can tare da zaid Emaar's da kuma arms da dama shima yana a cikin masarautar...... _Bayan kwana_ Alhamdulillah zuwa yanzun oum tana shashinta ta warware dama shock ne har yau babu wanda ya sake ganin me martaba AK ya kasa ya tsare a halin yanzun ma yana part ɗinsa. Kuma babu mahaluƙin da yayi gigin zuwa ko kofar sashen. Sosae fulani tayi jinyar merrah kuma itama oum ɗin bawai ganinta tayi ba tunda itama kusan a kwancen take. Zaune suke su duka A ƙayataccen palon oum ɗin domin yin dinner, Ak da zaid ne kawai babu se merrah da ba kowane yasan da zuwantaba ita dama. Fulani ce ta ɗan dubi jesrah tare da fadin "Kije ɗaki ki tahomin da baƙuwa" Da mamaki ta ɗan dubi kakar nata tare da faɗin "baƙuwa kuma grenny?" "Ehhhhhh zakije ko tsareni da idon zaki tsaya na aiki uwarki tunda ita na isa da ita!" Tsammmm ta miƙe domin tasan halin kakar nasu ba wasa take dasu ba. Babu jimawa kuwa sai gata riƙe da hannun meerah. A sanyaye ta zaune kan kujerar data saura ita kaɗai wacce take fuskantar kujerar da oum take zaune kai tsaye. Gaisar da duka mutanen palon tayi wanda ya sanya oum ta kusan kwarewa da tea ɗin da take sha, wani irin ɗago kanta tayi daidai meerah na sake ɗagowa tana me sake gaisar da oum ɗin ganin kamar ko bata jita bane. Wani irin tarine ya sarƙeta idanunta kafe akan merrah ɗin. Da sauri zaid ya ɓalle gorar ruwa yana bata a baki tare da dan buga bayanta kaɗan, Mahaifiyarta ta kalla tare da faɗin "Mommah wannan ai DID...... Saurim katseta fulanin tayi ta hanyar faɗin "eat itt, yanzu loƙacine na dinner bana magana ba ok?" Duk yadda taso ci gaba dayin dinner ɗin kasawa tayi dole itama fulanin ta miƙe tana me mata magana data bita zuwa ɗakin data sauƙa. Magana sukayi sosae wanda sai faman ɗaga kai oum take tamkar wata kaɗan garuwa, sun jima kafin ta fito tare da kama hannun meerah tana faɗin "Yarinya na muje mu sake gaisawa ki bani labarin ƙasata" Ita dai merrah cike da kunya duk wannan zafin kan ya tafi nashi wuri na wani ɗan loƙaci. Itane tayi ta janta da fira harta samh taɗan sake idan ta mata tambaya daƙyar take bata amsa. Amma kuma mamaki sosae take da ganin matar domin ka tsaye fuskan wancan tantirin na ƙasar Nigeria take a face na matar, saidai tasan gari banban Allah ɗaya domin babu ta yacce za'ai wannan kamilallar matar tama haɗa jini da wancan da satar mutane kawai ya iya, kuma ma tasan me zai kawo wancan babban criminals ɗin cikin ƙasar nan kuma ma har gidan sarauta me girma irin wannan. Sallar zuhr itane ta fito da meerah daga sashen oum. Bisa taimakon jesra da kawai taji merrah ɗin ta shiga ranta kai tsaye ta komar da ita har sashen da fulani take. Itama anan tayi sallar nan suka fada fira bata sake jin ƙaunar meerah ɗin ba sai da taji ashe itama jornalish ce wato ƴar jjarida, Dan duban Fulani tayi fuskanta na bayyana zumiɗinta ta furta "Ayya Mommah dama zaki bar mana merrah anan dan Allah!". Dake babu wanda yasan da batun auren sai Oum da shi kansa Boss ɗin wanda shi harma ya manta da wancan batun na Sarki suraj. "Gata nan dama ai tazo kenan tunda Yayanki take Aure" "Da gaske mommah wanne amma akie zaid aka aura mata ko?" "Abdoul-maleek, dai waye yaje nig a cikinsu?" Wani irin zaro ido waje Jesra tayi tana rufe bakinta da hanunnunta, "Wai kinanufin Gargalion din Oum ne yayi aure ba tare da mun sani?" Wata harara fulani ta watsa mata tana faɗin "Tunda kina matsayin uwar ne meza hana ki raba auren tunda baki sani ba" Daga haka ta miƙe tana bar musu ɗakin domin jirgin gobe zatabi Insha Allah ma kuwa. A ta can ɓangaren Moh jiddoh kuwa Abubuwane suke neman hargitsa mata kwakwalwar kanta, domin Abubuwan da suka faru cikin kwanaki biyun nan zuwa uku. Shin mene fassarar abinda ya faru da ita a daren ranar can? Shin me hakan ke nufi Kenan sanya idon da akama ma hassan Al-hassan ya ninka na baya. Da ita a ranar taso aika shi inda ba'a taɓa dawowa har gaban abada, me wannan nu'urar take nufi kenan wani ya ganta kome? Amma idan tai duna da ganin har yanzu babu wanda ya magantu a kan maganar sai wani sanyi ya ziyarci zuciyarta. Amma har yanzun abunda ya faru ya gaza barin tunaninta domin kamar tarihi na shirin maimaita kansa kenan, rabo da taji irin wannan yanayin tun a sadda da ɓatar da _AYESHERH_ babbar ƴar sarki Hassan Al-hassan ta farko. A ranar da tabar cikin masarautar a ranar akayi makamancin irin wannan yanayin idan lissafint ya tafi daidai kenan yau kimanin shekaru ɗɗaɗɗai har Hamsin da arba'n da shida kenan. A fili ta furta "me yasa tunanin yaƙi barin raina ne?" Haka dai tayi ta tunane abubuwa maban banta na mata kai kawo a tsakar kanta. Zumbir ta miƙe tamkar wacce aka zabura ta firta "JADDERN ASHAAN" Fita tayi a duhun magrib ɗin cikin shigar ɓatta kama kamar yadda ta saba. Wani surƙiƙin yankakken daji ta nufa na wani shashi daga cikin masarautar. Tayi nisa sosae ta tsinkayi muryan mahboob ata bayanta yana faɗin "Kai waye wannan tsaya anan, Ko waye kada ya kuskura yayi ƴunƙurin guduwa domin zan saki Nightingale, da Rhino da pig tare da unicorn su yagalgalamin namansa" Ɓari jikin moh jiddo ya ɗauka cikin tsantsan tashin hankali mara misaltuwa tasan ba shiri take da mahboob ba bare ya fuskanceta,ta kuma san tana gudu zai saki su pig ɗin kamar yadda yayi alƙawari. Cikin dakewa da kuma kame fuska tana dawo da ainihinta na jiddoh ta tsaya cahkkkk. Cikin wani irin shegen tuggu ta taryi numfashinsa tare da faɗin. "Taya zaka saye da haka ita dama kuskuren kunya ai da hauka ake naɗeta, wato fahimta kayi da ina bibiye dakai shine zaka wayance da faɗar haka! Idan baka sakar min suba kaiba haifaffe bane a cikin _ASAAD EMAAR's_ ubanka da yake gudun mahaifarsa dan ubanka da uwarka _SOFIYYERH ANAAN_" A gabanta yaja ga tsaya riƙe da ƙugu kallonta yayi daga sama zuwa ƙasa kana ya fesar da iska yana me faɗin cewa "Ai shi ba lusari bane da zai zauna zaman dogaro dana wasu, neman halak ɗinsa yake kinga kuwa babu laifi da bai zauna zaman jiran tsammanin na wani zuciyarsa a tsaye take shi ƙamm Kuma zaman. _ENGLAND_ yan zun ya fara muje kuma ko yanda babu kowa na ɓalla ƙafafuwanki na zubar anan" "Tirrr da haihuwar ɗa irinka wllh Assad ya haifamin masifa har abada jinin uwarka Sofiyyerh da jinin Maryam ba alkhairi bane a gareni masifa ne ku a cikin rayuwata" Kota kanta baibi ba haka dole don kaucema zargi tabi bayansa suna komawa ta barma gobe. Washe gari jirgin fulani ya lula bayan ta sake duba jikin me martaba da sukayi magana sosae da shi, Anan ta tajama Ak mugun gargaɗi akan matarshi. Shi kallon basu da hankali daga ita har mijin nata ma yake musu yasan kawai gigin tsufane ya fara kamasu. In banda haka Shi me zeyi da wata mace kuma ai ya ɗauka dan jin daɗi da samun nutsuwa ake yin auren?, to shi kuma duk baya da buƙatar hakan wine ɗinsa tafiye masa komai na cikin duniyar idan aka ɗauke mahaifansa. Dan haka ko maganar bebe wani muhimmanci ba yace koma wace idan ta gaji da zama tama ware da ƙafarta, Shida kansa ya kaita airpot zayd suraj nta famar tsokanarsa yana cewa kardai daga baya ya kwarema matarsa kuma yazo yana musu mimison goɗiya wllh ubanshi zasuci, haka jirginsu su fulani ya tashi cike da kewar ƴarta........ A gimtae *BY AMMEY LAYLERH* *🦅 MIKIYA 🦅* _A wonderful world & Special anti terroRism squad_ ____________________ *MARYAM NASEER MIRRAH* ~AMMEY LAYLERH ✍️~ ✯ *~🌠 JAJIRTATTU WRITER'S ASS.... 💫~* BOOK Two…………………………񆬍✍ 7&8 ♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡ # The friendship # Romance scene # His bloved_friend Meerah # Meerah Ak drama's ♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡ _NIGERA'n_ ~Lagos~ Tunda Isa manu yaji abinda ɗan nasa ya faɗa ya tattare nasa ya nasa ya gudu daga gidan baki ɗaya, Idan ya gama haukar tasa inyaso daga baya sun fuskanci juna, Amma kuma saidai me? Washe garin ranar sai labarin yasha banban.domin kuwa kai tsaye gidajen jarudu suka juya labarin kamewar da mom surry tasa aka mai da wani labarin na daban. _A wayewar garin yau kahadi mun tashine da rikicin kame babban ɗan wannan shahararren uban ƴan siyar wato Isa manu, bisa auren manufa da sukaso yi da wannan shahararriya fitacciyar ƴar jaridar wato, _MARYAM ABDULLAHI GWANI_ {MERRAH}. Wanda kai tsaye black mailing mahaifinta yaso yi tunda kowa yasan malam Abdullahi gwani babban malamine. Don dama bayau manyan ƙasarmu suka saba blackmailer's na mutane ba saidai kuma shi Allah ba azzalumin bawansa bane dan haka ma shine ya kuɓutar da merrah daga sharrinsu, ganin basu sami cikon burinsu bane ya sanya babban ɗan nasa yunƙurin kashe ƴar yayarsa da aka misanya masa da ita a matsayin Merrah ɗin..._ Wannan labarin da isa manu ya riska a washe garin ranar shi yafi komai ɗaga masa hankali.domin tuni labarin ya zama shine very latest a safiyar ranar, mantawa yayi da komi yaje har station ɗin hankali tashe domin ganawa da ɗan nasa, sai de amma sammm salman ya hana uban nashi ganinsa. Shi kuwa isa manu babban burinsa kawai so yake yaji daga bakin ubanwa waɗannan maganganun suka fito, domin tsananin tashin hankalin da yake a ciki yafi gaban kwatance. Haka yabar station ɗin hankali tashe kai tsaye babban gidan gonarsa ya wuce domin tattaunawa da ƙashin bayansa masu cin mushe tare masu fuska biyu a cikin al'umma....._ Daga nan kuma suka saki duk wani baɗakalar party'n da su salman suka gudanar tun ana saura kwana biyar bikin. Har dama becholer's night ɗin da sukayi wanda yafi ko wanne haramci tunda buguwane sukayi sosae tare da romance na ƴan matansu. _MOm surry_ (Hajiya Nafisa) Wata kafurar dariya ta kwashe da ita tare da doka ƙafa harda su riƙe ciki a loƙacin da take ganin labaran data tsara kai tsaye ta fiya maƙudan kuɗaɗe domin a fitar da labarin, "Koya yaci tuwa dani! Hhhhhhhhhhh ba kunce ku ƴan iska bane wllh inhar ba zaku risina ba yanzu wasan ya fara. Gashi tun a zagayen farko ni ce winner's idan kun shirya muje zuwa a sannu zanta bankaɗo manyan sirrika ina tonawa Hadiza kiyi haƙuri dolece ta sanyani hakan" Wani murmushin kina kasheni da salonki mom Surry ta jefi mahaifiyarta dashi, hannu ta bata suka kashe tana me cewa. "Farin cikinki a rayuwata shine gaba da komai shalele! Ki rubuta ki ajje salman isa manu har gaban abada naki ne ke kaɗan ki indai ina raye. Ba tare dako kishiya yayi yunƙurin yi miki ba yadda ni kaɗai na rayu da mahaifinki don haka kema ke kaɗai zaki rayu a naki gidan kiyi yadda kikeso da gidan dama me gidan gaba ɗaya" "I sonki mommana!" Surry ta faɗi tana me rungume mahaifiyar nata dan tapping gadon bayanta ta shiga tana furta. "Wannan alƙawarinane Shalelen mommah kar kiji komai" Acan gidansu salman kuwa idan hankalin Mum salman yayi dubu to a tashe yake, ganin ɗan nata a hannun hukuma domin sammm ita bata da masaniya akan auren manufan da mahaifinsa yayi niyar masa da yarinyar kawai dai abinda ta sani tasan bata son aurenshi da ita yarinyar har cikin zuciyarta domin haka kawai taji babu alkhairi a auren. Sosai hankalin Malam Abdullahi ma ya sake tashi, kenan ta tabbata Allah tseratar masa da ƴarsa yayi daya aiko masa da tsohon abokinsa ta hanyar nemawa jijinsa aurenta. Su kuwa sauran matan gidan da haryau sun gaza gano wanda aka ɗaurama meerah ɗin aure dashi sshine yafi komai soya zuciyarsu. Tunda malam Abdullahi'n be faɗa musu ba suma sai bayan ɗaurin Allah ya sheda musu cewar Allag beyi da salman ba amma Alhamdulillah basu tozarta ba domin kai tsaye wani tsohon abokinsa da dama nemarwa jikinsa auren yazo ya tarar da wannan matsalar yace kawai a daura auren a take. Wanda dama Malam Abdullahi'n yana cikin tashin hankaline domin ana dab da ɗaurin auren aka bayyana masa wasu shegun miyagun halayyar salman ɗin, yana cikin alhinin ne kuma Allah ya kawo masa mafita da ɗauki ta hanyar ɗaura mata auren kai tsaye ba tare da fuskantar wani tashin hankali ba. Wannan shine ainihin abinda suka sani kaɗai. Kuma duk iya kissa da kisisinarsu sun gaza gano mijin da aka ɗaurama merrah aure dashi kakaf garin lagos, sun kuma gaza gano wanene tsohon abokinsan daya ambata musu....... Anne kuwa baka isa gane ainihin abinda ke rai da ruhinta ba. Abinda ta sani kawai shine banbancin bugun zuciyarta daya sauya akan yadda take fuskanta akan auren salman, a loƙacin da malam gake me sanar da ita ga ainihin abinda ke faruwa a taje taji bugun zuciyanta yana sanjawa da wani irin sanyi sanyi Me kama duka sassan jiki a hankali. Toshe kunnuwanta tayi ga duk abinda yake shige da fice akan lamarin auren merrah ɗin. Domin taji nutsuwa kam ba ƙarya akan shi wannan auren nata na yanzu akan na baya, hakan yasa ta shiga binta da tarin adda'_oin kariya a duk inda take wannan kenan. Tana tsaye daga tacan bayan ƙofar kitchen take leƙen Mum salman dake zaune ta rafka uban tagumi. "Ai kaɗan ma kuka gani don baku ga komai idan har ban wargaza wannan ahaliba niɗin ba wushiyatu bace" zeey ta faɗi tana me sakin wata shegiyar dariya ƙasa². Kamar wanda aka hankaɗo sai gashi ya faɗo ɗakin babu ko sallama. Da sauri ta miƙe tana taryarshi tare da faɗin, "Aha Ina salman ɗin kuma Alhaji?" "Hmmmmmmm" ya saki wata ajiyar zuciya yana zama tare da zame hulan kanshi yana firfita da ita, "Alhaji magana fa nake ma! So nake ka warware min komi domin ni kaina a kulle yake da wannan batun, kana ina ita surayya'n ko duka aka haɗa aka tafi dasu?" Ta sake jeho masa wata tambayar ganin me tankata ata farkon ba, "Aike zan tambaya tunda kin haɗa baki keda ƴar uwarki kunci amanata,wllh Hadizah kiji tsoron Allah ai dama nasan tunda baki so aurensa da merrah ba dole zaki ɓata!. Saidai banyi zaton da wuri haka ba tunda muma amfaninta kaɗan ne a garemu, daga inda muka gama da ita jefarta zamu a bolar da muka tsinta, Amma shashashan shirmenki ya ɓata komai Hadizah" "Aika sake rufenin ne Alhaji kenan dai ta tabbata auren manufar kuka so yi da ita yarinyar kenan?" Sammm isa manu ma ya gaza bata amsar komi, domin wani irin turiri zuciyarsa ke may ta tabbata dai kenan dole akwai wanda ke bibiye da al'amuransu, Lallai yayi sake da yawa amma ba komi hakan ma tamkar sun zaburar dashi ne. Duk da yadda mum ke masa magana shareta yayi upsaid's nashi ya nufa yana tsane uban zufar dake keto mishi, harta ɗau hanyar saman itama domin bin bayasan sai kuma tayi saurin juyawa tana me nufar bedroom nata car key nata ta ɗauka tare da fita waje, Cikin wata dallekiyar Mwb ta faɗa tun kamin ta isa get take danna hong da ƙarfi don kai tsaye tanason suyi magana da Addarta ne Mom surry. Zeey na ganin fitar mum tayi wuf tana me nufar saman Isa manh. Yana tsaka da wayarsa yaji ƙarar door handle ɗin da aka taɓa saurin janye wayan yayi tare da katsewa ganin zeey ce, wata doguwar ijiyar zuciya ya sauƙe wani munafikin murmushi ta sakar masa tana ƙarasowa inda yake. Hannu ya ware maga a take kuwa ta faɗa jikinsa Hannuwansa ya sanya yana zagayeta tare da tambayarta. "Ta fita ne me gidan?" Ɗan ɓata fuska zeey tayi tare gyada mai kai, kumatunta ya lakata cike da ssheƙiyanci ya furta, "Yau kenan anji tausayina za'a kula dani uhum?" Wata shegiyar hararan gefen ido ta sakimmai a ɓoye daga nan suka shiga sheƙe ayarsu a ɗakin Aurensa na sunnah... _KUWAIT★_ The third season of *Winter Wonderland #EMAAR's* has kicked off, offering a unique winter experience that combines entertainment and fun activities for the entire family. #الكويت *UMAYMAH POV* Zaune takai wani irin zafi take ji yana ratsa ta tun daga tafin ƙafarta har zuwa tsaƙiyar kwanyarta, dalilin hakan nema ya sanya mata karkarwar jiki tamkar wacce ta ji kiɗan gangi. Wanda hakan ne ya haifar mata da gumin da ke ttsatssafo mata a kowacce kafar da ke cikin ilahirin jikinta. Ba yau ne karo na farko da hakan ya taɓa faruwa da ita ba, sai dai a wannan karon ji take tamkar an saka ta a tukunya ana dafa naman jikinta da tafashashshen ruwan zafi ne. Da ɗan ƙarfi ta ɗan ciji ƙasan laɓɓanta tana yarfe hannuwa haɗe da lumshe idanunta da takejin su tamkar a watsa mata barkono a ciki tsabar zafin da suke mata. Amintacciyar hadimarta beenanzer da ke bayanta tana mata fifita cikin ƙwarewa a iya makirci ta sake rusunar da kanta ƙass. "Hutawarki lafiya uwar ɗakina takawarki lafiya uwar magajin sarautar Emaar's zinariyar sarautar Emaar's haskenki bai tsaya iya shi kaɗai ba kin haske lungu da saƙon cikin Masarauta. Ina gwanar wani ga tawa! Kin yi taki kin yi ta kowa garnaƙaƙin dutse kike kowa yay karo da ke shi ka faɗi! Hadari malafar duniya kenan. ki kwantar da min da hankalinki Auren da suka ɗaura masa na bazata hakan ba zai sanja komi ɗin a yadda kika san shiba, kin manta kece uwar maza a wannan masarauta? Kin manta babu me gigin ɗaukar ɗaya daga cikin waɗan nan watsatstsun yaran ya basu sarautar Emaar's. Domin kowa shedane na sanin cewar suɗin ba kowa bane su facen drinker's Humanzer's wanda dattin zina da giya suka gama musu fenti, Ki ɗauki wannan auren ba'a bakin komai ki ɗauke shi a matsayin matacce! shuɗaɗɗe...... Wani irin juyowa ga hadimar tata tayi cikin wani irin zallar fusata ta furta. "Kada in damu fa kike cewa beenanzer? Kinsan kuwa irin tashin hankali da nake ciki duk sanda na buɗi idanuna na kalli waɗan nan shegun yaran? A matsayin ƴaƴan sarki hassan Al-hassan wanda sune magadan sarautar Emaar's ko kin mance sune manyan ƴaƴan maza a masarautar nan? shin baki ganin iyakata da mulki sai dai gani sai hange tunda sune manya akan nawa ƴaƴan? ko baki ga yadda komai ya fara juye min ba? Shi wannan tantiran ya ɗauke uban nashi da ina dab da cikar burina Amma shegiyar tsohuwar ta ɓata min aiki, Kuma sama taka an kuma shammatata ta hanyar ɗaura masa aure wanda shine babbar barana a gareni! Ya kike son nayi? Zuciyata na dab da tsayawa da aiki beenah! A ko wanne hali a ko wanne irin yanayi inason a sake tarwatsa ahalin Maryam inba ta kama da ɓatarwa tamkar shekarun baya da aka ɓatar da ƴar Razeenerh to suma a ɓatar min dasu,yanda ko labarinsu ba za'a sake tayarwa bare na baya su riska tamkar da yadda akama Eesha Emaar's" Cike da wani irin tsoro jesrah taja da baya tana me toshe bakinta da hannuwanta, cike da tashin hankali da tsananin tsoro ta zaro ido da tarin mamaki bata gama dawowa hayyacinta ba taji Mum Mandood na sake faɗin. "Wallahi tallahi billahil azeem zanyi komai dan ganin bayan Maryam da yaranta, zanyi duk abinda ya kama domin in kauda _ABDOUL-MALEEK da kuma zAID_ A matsayin magadan sarautar Emaar's masu jiran gado, dan wlh Allah a wannan karon zan iya kashesu bawai ɓata su a matsayin mashaya da kuma maneman mata ba, domin kuwa wannan rana tana ɗaya daga cikin abinda yasa nayi bore a shekarun baya. Amma sai gashi nayi GUDUN ƘADDARAR wannan rana me kama da irin yau!. kuma sai gashi yanzun alamu na gwada min dukkan wani dagewa da taƙarƙarewata wajen gujewa wannan rana irin haka saidai kamar ma biye take da nawa sawayen ƙafa da ƙafa domin al'amura ne keta faman yimin warwara ya zamanane kamar ina dufka ana min warwara. Loƙacin mutuwar _JADDERN ASHAAN_ yayi ba tare da wannn kwalmaɗaɗɗiyar tsohuwar ta sani a tunaninta ita kaɗaice me basira har wani tinƙaho take da babu wanda yasan ida jaddern ashaan take! Bayan kuma ta haifi ɗa mara amfani lusari Tirr da mutum me irin halin Hussein..... Cikin tsananin kaɗuwa jesrah ta juya da sassarfa tana tafiya da baya baya harta samu tabar sassan Mummy Mandood Iska kawai take fesarwa Sam tama rasa ma wanne irin tunani zatayi,gaba ɗaya kwanyarta ta toshe Shin su waye waɗannan Eesherh da kuma jaddern ashaan? Tambayar da tazo ta mata tsai a zuciya kenan, ko gabanta bata gani babban burinta kawai ta ga Oum ɗinta domin tasan ita tana da amsar duka waɗan nan tambayoyin nata. Karon da taji tayi da mutum ne ya sanyata saurin cin birki, itama a nata ɓangaren da sauri merrah taja nata birkin dafe da goshi. "Wayyo kin fasa min goshi" Ta faɗi tana me duban jesrah ɗin da sukaci karo a hanyar shigarta palon Oum ita zata fito ita kuma zata shiga. Dake ba'a cikin nutsuwanta take bane ya sanya ta furta. "Sorry Habeebty banganine sosae" tana faɗar hakan ta shige palon Oum ɗin.... Oum dake tsaye har yanzun bayan fitan merrah ne tayi saurin duban bakin ƙofan, ganin saɓanin tunaninta ne ya sanya ta faɗin, "Jesrah bakin fita wurin aiki bane kamm?" Kanta take girgiza mata tana kuma nufota ɗan daidaita numfashinta dake seezing tayi tana dannar setin haert nata tare da furta. "Oum Su waye _JADDERN ASHAAN_ da kuma _Eesherh_ ?" Da wanj irin masifar karfi Oum ta juyo tare da riƙo hannuwan jesra ɗin cije da matsanancin tashin hankali ta fuskanceta dakyau tare da faɗin. "A ina kika ji? Waye kuma Jaddeern Ashaan? Easher kuma ƴ.. Ƴar...... Sai kuma ta ƙarasa furta abinda take son faɗin sakamon zuciyarta da taji ya mata wani irin mugun nauyi, tare da hautsuno mata da wasu shuɗaɗɗun al'amura maban banta cikin abinda bai wuce second biyu ba. Zaune takai gefen haɗaɗɗen royal bed nata tare da matse hannun jesrah ɗin cikin nata tana fesar da numfashin daya mata tsai a ƙahon zuciya. "Komai ya kusa bayyana kansa, komai kuma ya kusan zama tarihi Insha Allah kiyi shiru da bakinki Allah yana daga bayan me gaskiya" Haka kaɗai Oum ta faɗim ma jes tace ta fita aikinta Allah ya bada sa'a jiki a sanyaye ta fita ba tare data fashimci komai ɗin da taso ffashimta, amma ba komi insha Allah a matsayinta na ƴar jarida dole sai tasan wani abu daga cikin labarin kafin bayyanar komai ɗin kamar yadda oum ɗinta ta fadin mata...... Wata nannauyar ajiyar zuciya ta sake a loƙacin data gama tabbarwa da cewa jesrah tabar room ɗin baki ɗaya Goshinta takai ƙasa tare da furta. "Ya wadud,Ya zul'arshin makin, Allahu ahad kaci gaba da ƙare wannan bayin naka daga duk wani sharrin me sharri. Ya Rabbis samawati wal'ard karkaci gaba dabe mugyaye damar da zasuci gaba da zalumtar keɓantattun bayinka, Allahu kaine Allah kaine me yadda kaso a duk sadda kaso ɗin kuwa Allah ka mana maganin Azzaluman da burinsu suci zalinmu su zalumcemu Ya ilahi ya mujibud da'awati Allah kare ɗaukakin keɓantattun bayinka wanda basuji ba basu gani ba, Allah ka mana maganin wanda suke ganin sunfi ƙarfinmu Allah ka zarta da ikonko na _KUN FA YAKUN_ akansu ya Allah!!!" Oum takai ƙarshen adda'ar nata tana me fashewa da wani iri kasalallen kuka irin wanda ya daɗe yana cin zuciyar nan. ★★★ _AK_ Gaba ɗaya ɗakin tsit yake daga sautin karatun Afif muhd taj bakajin komai a room ɗin sai iskan dake kaɗawa irin ta farkon daminar nan da kuma ta sanyin AC kawai kakeju. Sai wani irin ƙamshin Air freshsheners da turarukaan wuta masu daɗi da babu jimawa aka gyara may, Ɗakine me girman gaske dake ɗauke da setin royel furnitures masu tsananin kyawun gaske White colour sai ɗan adon milk color daya aka musu. Daga ta nan bakin bed ɗin wani haɗaɗɗen kuwait carpet ne me tsananin laushi da aka shimfiɗa wanda yakai har tsaƙiyar ɗakin, daga gefen window's kuma wata keɓantacciyar kuwait sofa ce Ajiye da ƙaramin fridge. daga gefen mirror kuma wani babban table ne da aka jera littattafan Addini shimili guda gasunan, daga ta gefen gabas akayi wani zagayyen wuri na musamman wanda ke shimefiɗe da wata kalan lallausan praymed me taushin tsiya, sai wasu zagayayyun kuwait decoration's irin masu haskaka room ɗin, sammm ɗakin baya da woni tarkace haka yake simple gwanin birgewa wanda mutum zaiyi normal real life nashi cike da bada cikakkar nutsuwa. Agogon ɗakin ne ya buga ƙarfe 11:31 am na ranar yau Monday daidai bjgawn agogon ɗakin yayi daidai da Mirza handle na ƙofar bathroom ɗin da Ak yayi, Anutse ya fara ɗora santaleliyar ƙafarsa me cike da gargasan gashi baƙi siɗik akan ƙaramin carpet ɗin dake shimfiɗe bakin ƙofar bathroom ɗin. kafin ya Ida fitowa gaba ɗaya ya a nutse ya fara taka sawayensa cike da nutsuwa take ɗakin ya gauraye da ƙamshin shower jal ɗin da yayi wanka dashi. Ahankali ya nufi gaban dressing mirror yana ɗaure da towel navy blue iya ƙugunsa da yama wani irin loko lokon ɗauri, sai wani milk saman wuyansa yana goge ruwan jikinsa dake yarara lafiyayyar tsayayyen jijinsa me jini a jika sai faman walainiya take tamkar woni beby sabuwan haihuwa. Wannan fuskar da cikar kamala mai nuna barazana wa maƙiyinsa dole ne ya yarda yaci wannan suna na jarumi kuma ingarman namiji me ji tashen samartaka wanta jinin mulki ya gama ginashi, zuciyar nan nasa samm babu daɗi baƙar zuciya ta ɗan motsa da dukkan alamu kenan yau don a matuƙar haɗe take. Ba kuma komai ne ya fusatar dashi ba sai zancen matar shi da Oum ta masa a daren jiy!, wani ɗan numfashi ya sauƙe a karo na farko tare da ware lumsassun idanunsa yana me sauƙe ganinsa saman Abubuwansa da yake da tabbacin Zaid ne ya kawo mishi. Komai yake yi cikin tacin zuciya yake tsafff ya gama shirya kansa cikin wasu haɗaɗɗun egyptanian riga da wando ya sanya sky blue, pcarp nashi ya zira inda farar lafayayyar cutie face nashi ta ƙara fidda ainihin taswirar kyawu da kuma zatinsa. A natse ya isa gaban Iphone nashi inda sautin karatun ke fita take karatun kuma ya tsaya sakamakon shigowan ƙira ɗan lumshe Ido yayi ya kuma sake buɗewa ya kalli agogon dake manne jikin bango, red lips nashi ya ɗan ciza bada yawa ba yana ɗaukan phone in dama yasan ƙiran bazai wuce Oum nashi bace, ba tare daya ɗauka wayan ba ya nufi hanyan fita, kamar yadda yana yinsa na rashin fara'a yake haka yafito daga cikin ɗakin hannunsa riƙe da key nashi na Keken da yake son hawansa yau. Drectly Sassanta ya fara nufa tana zaune akan wata royal sofa ruwan zuma, tayi crossing ƙafafunta wanda da duk alamu a wurintane Ak namu yayi gado aha. A nutse ya shigo cikin nutsuwarsa da deep voice ɗin nan tasa ya furta "Assalamu Alaikum!" "Wa'alaikas salam habeebty" Zama yayi daga gefen ƙafafunta yana me ɗora kansa saman ƙafafunta cike da cunkushewar zuciya ya furta, "Barka da safiya Oummuna" Gashin kansa ta ɗan shafa kasancewar ya zame pcarp ɗin, kafin a tausashe ta amsa shi cike da kulawa. Apple ya ɗauka daga jerin fruit ɗin dake shaƙe a gabanta. Babu jimawa saiga zaid shima wata harara ya cillama Ak ɗin yana ɗauke kai daga kallonsa, shima yi yayi tamkar be ganshi ba ya zauna aka fara break ɗin dashi. Shigowan jesrah kenan ko zama bata samu ikon yiba oum ta furta, "Maza je kizo min da zauj Al-maleek!" Rassssss gabansa ya bada sautin bugu yana tsayawa daga shan coffee ɗin da yake a tsime, babu jimawa sai gata ta dawo zama tayi gefe da Ak tana faɗin. "Oum bacci ta koma mebi ta gaji ne kinsan yau ita kaɗaine tayi duka dinner ɗin nan" kai kawai ta ta ɗaga mata suna ci gaba dacin kayan karinsu.Ak kuwa wata ɓoyayyar ajiyar zuciya ya sauƙe yana ci gaba da shan coffee ɗin da ya masa daɗi sosai, bayan da suka kammala yin dinner ɗin jesra ta fita cikin sauriri domin yau ta kusa yin late nema. Zaid ne ya ɗan dubi oum a shogoɓe yana karyar da wuyansa gefe cikin ɗan tura baki kaɗan ya furta "Oum ni yaushe zaki min auren ne tunda kimma biyuna?" Wata daƙuwa oum tama zaid ɗin tare da ranƙwashin kansa da samm baya saka hula ko wacce iri, sake tura bakin gaba yayi yana me sake faɗin. "Kinga dama gobe birthday na don haka saiki shirya min suprise mata a maimakon kyautan da zaki min really?" Yana faɗin haka ya kwasa da ɗan gudu gudun kada yanzu kuma yasha dundu, saman lafiyayyan gadonsa ya faɗa tare da ciro wayansa yana buɗe datan wayan domin tunawa duk wani clips nasu cewar gobene fa birthday nashi.......... To ai shikenan saimu gimtse anan kawai Sai munzo taya murnan birthday koda kuwa a gayyar soɗi ne aha koba haka ba my FAN'S??? *BY AMMEYLAYLERH* *🦅 MIKIYA 🦅* _A wonderful world & Special anti terroRism squad_ ____________________ *MARYAM NASEER MIRRAH* ~AMMEY LAYLERH ✍️~ ✯ *~🌠 JAJIRTATTU WRITER'S ASS.... 💫~* BOOK Two…………………………񆬍✍ 9&10 ♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡ **☆✭ ★ You Are My Dream Come True _Meerah AK 😊🙃🥰😍_** Kai tsaye status yayi da, _My people tomorrow is my birthday my celebration comin at 8:10 pm O'clock Wow my people have a crucial celebration at moment time,Happy and axcited to u all_ Kamar ƙiftawar ido da bismillah sai gashi mutane har sun fara replying nashi. Mutum na farko daya fara turo masa saƙo shine Afif taj babban abokinsa da _Happy birthday to my incredible dud in life, On this special day, I want to take a moment to appreciate the unbreakable bond we share. From childhood memories to adult adventures, we've been through it all together. I am so grateful for the laughter, the tears, the late-night conversations, and the unconditional support. You are more than just a brother - you are my best friend, my confidant, and my guiding light. As we celebrate another year of ur life, I wish for you to have Joy that overflows from your heart ,Success that surpasses your wildest dreams, Love that surrounds you always, Health that keeps you strong and vibrantHappiness that fills every moment. May this new chapter bring you closer to your goals, your passions, and your heart's desires. May you continue to grow, learn, and evolve into the amazing person you're meant to be. I am honored to be your ZAID EMAAR's partner in crime, and your forever friend. Here's to many more years of making memories, creating new experiences, and exploring life together. With all my love, appreciation, and well wishes, happy birthday once again dud 🎉_ Daga nan sakonnin mutane suke bude masa suna shigowa kai tsaye na taya shi murnar birthday nashi. Duddubawa ya shiga yi wasu ya amsa wasu kuma ya share ya ɗan 6ata loƙaci sosai akan wayan daga ƙarshe dai sai kashe duka wayoyinsa yayi. Yay bacci abinsa merai da lafiya. Bangaren Ak bayan kammala dinner nashi wani kai tsaya ya ɗauki luzury blue Kekensa yabar entrance na masarautan ma baki ɗaya. Ta wata boyayyar hanya yabi gudun kada waɗan nan natattun suce zasu bishi, Saidai ashe yayi na banza ne domin loƙacin da yake dab da fita wani soldier ya ganshi. A take ya ƙira wasu suka mara may baya amma bata yanda zai gane ba. Daga cann ƙasan ranshi yake jin wani irin boyayyen farin cikin da besan ko daga ina yake ba, Yawo kawai abinsa yake akan shimfiɗeɗiyar kwaltan. Kai tsaye wani Haɗaɗɗen estate ya nufa a anguwar _MASHATLE SHUWAIK_ Estate ne wanda yayi fice yayi shura a birnin ƙasar nasu, anguwace ta manyan mutane kebantattu daga cikin tsiraran mutane ne ke rayuwa a cikin estate ɗin. A wani haɗaɗɗe tsararren dogon gini ya yatsa on tampring na duka finger's nashi biyar door glasses ɗin yayi. Saida suka tabbar da ya shige lafiya kana suka bayyana a gaban wurin suna zagaye ilahirin ginin don wanzar da tsaron lafiyansa. Da kekensa yaci gaba da tafiya a titin gidan da ya wani irin bala'in haɗuwa kamar ba gobe. Ya ilahi wani irin tsararren gidane me ɗauke da ground floor, private entrance , big private garden , 4 bedrooms , big lobby, big maid room, kitchen, 3 bathrooms, private 2 shaded car parking, no landlord lives in the house. Komai na gidan a nutse a kuma tsare haka yake. A wata ƙofar mashiga ya dakata wacce gaba ɗayanta ta kasance ting tihgt ce, sai ruwa da hadarin dubai tsaruwan wurin ya bada wata sassanyar nusassiyar iskane ke kaɗiwa a hankali wanda kai tsaye take tafiya da ƙamshin flower's ɗin da suka ma gidan dama estate ɗin ƙawanya. Nan ɗin ma dai on tampring nashi door handle in yayi. Da ƙafa yayi tafiya me ɗan zurfi kasancewar yau baya da buƙatan hawa lifp. Ci gaba yayi da tafiya da ƙafafunsa haka harya iska wani shegen ploor me azabar kyau da tsaruwan daya kusan tafiya da tunani. A wani entarnce door ya tsaya Akun da aka sanya domin be mutum umarnin shiga ne ta naɗi sautin amon murayansa kana ta bashi daman shiga, Ƙofar wata kuwait dooor flop dark room ce ta bayyana daga ƙasan kuwa farat ɗaya idan ka kalla kai tsaye zakace ruwane ya tare hanyar ga wanda be sani ba. Amma kai tsaye ga wanda ga sani kallo ɗaya zaima wurin ya gane cewan Opp water's tiles ne Malale a hanyan. {Lol😊😂☺ banda ƙauyenci su O'oh ahammmm Munje..... Ta maƙalƙaleni tana ihu da kururuwan waiya ruwa² itafa wllh ba zata shiga ruwa ba😎😎😎😎😫 dan haka masu tsoro close your Ido uhummmmm} Sanyin da yaji ya ratsa har tsakar tafin ƙafarsa ne ya sanya shi ɗan rumtse ido yana ɗan bata fuska tare da cizar ƙasan lips nashi ba da yawa ba, Sai kuma ya buɗe a hanzarce tuna ko a ina yake da wani irin sassarfa ya isa xuwa ga asalin bedroom ɗin domin ba ɗan ƙaramin missing nata yayi ba duk da kuwa cewar rana ɗaɗɗaice baya kallonta ta cikin cct fotage ɗin daya settinlyng da komai nashi. Harda ɗan guntun gudunsa ya isa ka dattijuwar dake zaune ta juya bayanta da dukkan alamu woni abu me muhimmanci take ko take dubawa. Ta baya ya ɗan yi hugging nata yana ɗora kansa akan bayanta. Alqur'anin da take karantawa ta ajje bayan kamar good 5mints da shigowansa, gashin kansa ta shafa yana me sauƙe wata boyayyar ijiyar zuciya. Jin ta taba shine ya bashi tabbacin takai kejin da take son kaiwa ɗinne domin kuwa tun a farkon shigowansa yaga tana karatun alqur'anin. "I miss u so much haskena!" Ak ya faɗi cikin wata kalon muryan da yau kaɗai ya bayyana raunina muraran. " and miss u shalelen Hasken haske!" Kamilallar voice nata ya bugi kunnuwansa, Ɗan lumshe idanunsa yai yana me jin zallar farin cikin ganinta cikin ƙoshin lafiya. "Ya yanayin jikin haskena yake?" Ya jefa mata wannan tambayar kai tsaye, "komai yana ta sake zama kamar a tarihi ne shalele, iyaka kulawanka kaɗai kan wanzar da samun cikakkar lafiyana hasken haske sai dai muce alhamdulillah, tun a nan zaka gane lafiya ba kamar baya ba da nake kan ganiyar hauk........ Kasa ƙarasawa tayi domin ta hanyar toshe mata bakin da yayi, domin a duniya ya tsani jin wannan kalmar daga wurin koma waye bare kuma daga bakinta. "O'ohh kina son zuciyan shalelenki ta buga ne kawai ko J..... Hasken shalele? Pls ki manta komai kamar komai ɗin bai taba faruwaba! Yanzun baga kinan ba darai da kuma lafiyankiba and ya kamata ki goge duka sauran memorie's ɗin daya saura a cikin brain naki hasken shalele right?" Sake shafan gashin kansa tayi tana jan kaɗan ba da yawa ba. "Alhandulillah Allah alhamdullilah I don't have enough words to thank u or described how am feeling right now after open my eyes and see me in front of the apple of my eyes the favourite part of me"Ak yasake furtawa yana juyowa yayi facing matar yana sakar mata wani lafiyayyen murmushinsa daba kowa ke samun kalansaba. Wani irin hawaye ne ya ziraro daga idanunta sanda taji yasake rungume ta sunfi 1mnt a haka sannan yayi breaking hug ɗin yana kama hannayenta yayi kissing nasu. Chaliey robbot ɗin dake kula da duk wani al'amura na gidan Ak ya ƙira cikin abinda bai gaza 3minst ba sai ga wani saƙagon robbot ya bayyana . wanda shi da kansa ya ƙirƙiri abinsa domin kulawa da lafiyan grennpa nashi domin bai yarda da kowa a fannin kula masa da hasken saba. Gidane ke6antacce da babu wani halitta da yasan yana da tun a loƙacin da ya kawota gidan. Komai dake wakana a gidan waɗan nan robbot ɗin sune ke aiwatarwa domin gudun kada aci amanarsa, ko'a ha'inceshi hatta da komai da komai sune suke kama daga kan kitchen har zuwa su moping, wanke² dadai sauransu. Da nu'urar jikinsa yayi amfani ya duba abinda yake son ya duba ɗin kana ya sallami chaliey. Babu jimawa saiga rakatun maganan Yesh,tare da zurat sun cika palon, "Ohh god!" Ya faɗi yana me zamewa ya kwanta don yasan halin yesh ba barinsa zaiyi ba shike nan, "Barka da xuwa babban aboki!"Robbot yesh ya faɗi . "Dud!" Ak ya ambaci sunan robbot ɗin yana me cewa. "Pls bansan stress ka barni kona maka filla² Ka tashi a aiki na ƙirƙiri Afuuh, kai ka tashi a aiki okoy?" Yanajin hakan tun be ƙarasa ba ya ɗauki hanyar barin bedroom ɗin yana daf da fita yace "Battery na yayi sanyi, kana plash nawa yana gaf da samun matsala ayi gaggawar sauyasu tare da charging piont na samu rauni ba dayawa ba kamar yadda nake d....... "Najiiiiii" Ak ya faɗi yana cewa "bani zanyi aikin ba chaliey zai chajeka!" ita kuwa dama zurat tuni tabar wurin. Daga nan baccin daya kwana biyu baiyi irinsaba yayi wuff dashi, Ido sosae dattijuwar ta zuba masa tare dajin wani mugun tausayinsa, "Kana ganin jarabawa yaro sannu ɗan baiwa" Cikin wani irin slow ya juyo da face nashi suwa kan fuskanta, sauƙo da idanuwansa kan fuskarta yayi kallon ta yake kamar ba gobe a hankali ya motsa bakinsa wanda nima da banji meya faɗa ba? wani guntun smiles ta saki tana me sake gyara mishi Konciyarshi, nan baccin gasken yazo yayi awon dashi. _Almost 2:37pm ★★★ A nutsensa ciki wannan yanayin na kamewa da muskilanci yake saƙƙowa a saman stairs ɗin, Sanye yake da 3q jeans black sae armless brown. Hangota yayi zaune cikin babban falon nata hannunta riƙe da mug tana sanye cikin wata doguwar rigar kuwait Jallabiya. Zana yayi a kusanta yana amsar mug ɗin tare da ɗan sipping shayin kaɗan bada yawa ba. "Kafito kenan?" ta faɗi tana kallonsa da kai ya amsa mata domin yana tashi yaji zuciyansa tamay nauyi, Zama kaɗan ya ƙara ya mata sallama ya fice bacin sun tattauna wasu muhimman sirrika. ★★★ _MOH JIDDOH_ "Haba jidd0h Ae tun asali ma laifinki ne da kika bari har ma ya kai tsawon wannan loƙacin muna sponsoring nasa da kinyi duk mai yiwuwa tun a baya kin sa an kawar dashi ne ae yanzu gashinan ya zame mana ƙarfen ƙafa shida shegun ƴaƴan san nan!. Yaufa kimanin 7 days kenan ko ikon ganinsa bamu da bare mu kawo ƙarshen wasan kowa ma ya huta!" "Bazaka gane ba Hussein na fika jin raɗaɗin hakan dahar na raini ɗan kishiyata a matsayin nawa ɗan! Sai yanzun nima nake sake tabbar dacewa ba ɗan ƙaramin ganganci nayi ba! Amma ba komi anzo ga6ar da dole su kwalba su bayyana domin kawo ƙarshen komai a yanxu bana da buƙatar sake jin komai ko ganin komai fa ce lalacewar family'n _JADDER'N ASHAAN_ Ina son kafin numfashinta na ƙarshe bayar ganganr jikinta ta ɗanɗani ɗaci da kuma azabar da hakan shine zaiyi sanadiyar bugawan zuciyarta. domin kuwa tana ji tana gani ɗan data haifa zaice ba itace uwarsa ba tare da shegun jikokinta. Ina buƙatar yau naje tare dakai domin kuwa shine na ƙarshe kuma ta fito kenan, A gaban idonta za'a harbe kan ɗanta bata ikon hanawa Hhhhhhhhhhhhhhhh.......... Ta sheƙe da wata kafurar dariya tana ƙarasa shigewa bedroom nata. ******** _NIGERIA'N_ *Lagos* ****************** _Mariya Kamaal_ Tana tsaye a kitchen sanye take da top irin wannan wanda daga ƙasansu ake ɗinkewa hakan yasa gefen cikinta yake a buɗe sai crazy 4½, shigowanta kenan kanta a kunce a nutse tasa hannu ta tattare shi ta sakashi cikin trap band Yunwa take ji sosae hakan ne ya sanyata dafa couscous jallop bata jima kuwa ta fito ajiyewa tayi a dinning Area tayi sama domin ɗaukar chocolate nata na gado batakai ga hawan stairs ɗinba aka danna bell. ''haiiii waye kuma yake ƙoƙarin shiga haƙƙin ni da kuma babynmu?" da yanayi na gajiya ta faɗa da kuma yunwar da take azalzalarta tana me yarfe hunnuwa jan ƙofar tayi da ɗan ƙarfi Tana sake ambatar, koma dai waye zai shiga hakkin babynmu wlh" "Baban babyn ya dawo domin sammm ya gaza samun nutsuwar zama ba tare daya sake jin dumin babyn da kuma maman babyn ba" Kamaal ya faɗi yana jawota zuwa cikin jikinsa. Ɗan bakinta ta tura sai kuma ta furta "yunwa mukeji first" "Aha go ahead muje na kula da maman baby kar yunwa ta kama min baby tun a ciki" Ɗan rufe idonta tayi alamarn kunya sai kuma tayi saurin janye jikinta tana wucewa gaba, "Ina kuma kike shirin zuwa haka?" ya tambayeta ganin tana ƙoƙarin hawa sama. "Zan ɗauko chocolate nawa ne fa!" "Dawo a nan wai ban hana shan zaƙin nan haka nan ba ne kammm?" Kwa6e fuskanta tayi kwalla na tarun mata "kuma fa kasan idan har bada chocolate naci ko miye ba ba zama yake mun a ciki ba zanyi aman sane Aiyn" "Mrs Aiyn dawo nace badai chocolate bane ganan wani nazo miki dashi" Ya faɗi yana tashi ya dawo da ita yana zaunar da ita kan ƙafafunsa... Shida kansa ya bata abincin duk lauma bayan laum saiya haɗa mata da wannan chocolate ɗin don haka shine wanzuwar zaman lafiyansu su duka tunda ta sami cikin nan kuwa. "Sannu da zuwa Aiyn" Ta furta bayan ta gama ƙoshi abinta tukunna. "Uyummmm saida kika gama cika ciki kana kika tuna damin sannun really?" "To ai zuwa loƙacin ko kallon gabana banyi sosae ne aiyn" Ɗan shafa gefen fuskanta yayi yana faɗin "Babyn Aiyn rigima" Haka dai suka shashance abinsu aikin dabai koma ba kenan. ★★★ Ta buɗe baki kenan da niyar sake wata maganar, amma maganar da maƙale a bakinta sakamakon tozali da idanuwanta suka mata da merrah. Wani irin tsuma tare da yankar zuciya ta tsinci kanta a ciki da kallon meerah ɗin, jinin jikinta kuwa a take ya shigawani irin hautsina mata wanda hakan kai tsaye ke tabbatar mata da tafasa jinin jikinta yake. Ido Oum ta kafe Mah dasu domin ganin reaction nata, Sammm ta gaza janye idanunta akan meerah ɗin da ƙyar ta samu ta fusgo kalmar "Easherh? DIDINA!!!" Da sauri itama merrah ɗin ta juyo da kanta zuwa inda tajiyo irin muryan Anne'nta masoyiyarta sakk. Itama chakkk ɗin ta tsaya tana kafe matar da ido babu wata tantama zata iya rantsewa wannan fuskan Anne'ntane wllh. Saidai ita wannan ɗin tsantsan hutu da jin dadi daya gama huda fatar jikinta da kuma tsananin hasken fatar ta. To amma wannan kamannin ai sunyi yawa kuma dai tasan Anne'nta bata da alaƙa da matar dake tsaye a gabanta. Domin kuwa tasan basa da alaƙar gari ɗaya ma bare kuma ta jini. Hannuwanta suna rawa ta matso ga Merrah ɗin tare da shafan fuskanta cikin wani irin raunin murya ta furta. "Irin kamar ki ɗaya da DIDINA! saidai a yanzu duk inda take nasan tafi haka zama ta iya haifar yake" Hannunta tasa tana kifewa saman na matar da ganinta ya bugar mata zuciya, wllh zata iya rantsewa da'@ Nig taga matar nan babu abinda zai hanata kamata tace itane mahaifiyar Anne'nta duk da kuwa cewan wannan matar baici ace ta haifi ya Annenta ba. Muryanta yana rawa itama ta furta "Da'a ce a ƙasarmu na ganki babu abinda zai hanani cewa kene mahaifiyan Anne'ta" Saurin rungumeta Merrah Mah tayi tana furta "Allahu ahad!! Allahu ahaad!!! Wllh irin muryan Queen Lajja na ce dake" Kamar daga sama taji Mah taji muryan Oum tana faɗin. "Taya barewa zatai gudu ɗanta kuma yayi rarrafe ita ɗin JININKICE! Ƴar gidan Easher'nkice RAZEERNERH" Da wani irin bala'in ƙarfi ta sake rumgume Merrah ƙa ƙam a jikinta tana fashewa da wani mugun kukan daya kusan sarƙe numfashinta. "A ina? A ina MARYAM? Kar dai kice min itane MATAR ABDOUL-MAKEEK? Inkuwa hakane lallai Allah da girma yake kuma shine buwayi gagara misali shi yasa tun a ranan data sanwo ƙafanta cikin wannan gida bugun zuciyana ya sanja, Sanyin da nakeji a tare da Easherh na wllh shi naji tun a ranar" Sai kuma tayi shiru tana ɗan ɗago fuskan merrah idonta bai sauƙa akan komi ba sai kan wani ɗigo da yake kan gefen wuyan merrah ɗin wanda yake tamkar zanen tatto. Sake rungumeta tayi sai kuma sukayi luuuuuuu sakamon sumewar da Mah ɗin tayi. Merrah kuwa dama bata san mike faruwa ba ita dai tasan mafarkine kawai take wanda a cikin mafarkin jinta da ganinta suka jima da shuɗewa, shi yasa ma loƙacin da sukayi bayan itama tabi ta kawai a tunanin ta duk a cikin mafarkin ne Kafin takai ƙasa Oum tayi saurin tararsu itada Jesrah da shigiwarta kenan room ɗin Ak din don ganin Pa'pa'nta. Dawowarta daga wurin aiki kenan don Zaid ne ya isheta akan tayi maza ta dawi zata may wasu abubuwa kafin wannan kayan fushi da bacin ran ya dawo gidan wato AK. Tana zaune bata san sadda ta miƙe tsaye ba zumbir tana furta "Wacce Easher'n ?" Ta tambayi hadimar nata wanda dama shigowarta kenan ta dawo daga fitar da tayi tun da sanyin safiya. dog year rigace a jikinta abaya wacce aka narka manyan kuɗaɗe kafin a siyeta ,saikuma gyalenta data yane kanta sai jakarta da kuma takalminta suma duka designer ne. Damƙar wuyanta tayi tana me sake faɗin"Nace miki wacce Easher'n?,ba tambayarki nake bane wai?" Ta faɗa cikin ɗaga murya wanda hakan saida ya razana Hadimar daganin yanda yanayin Moh jiddon ya sanja loƙaci ɗaya. "Umm ummm dama dama..... "Ummm dama me ki buɗe baki kimin magana dama me? Ta faɗa tana sauƙe wani irin wahalallen numfashi mai nauyi haɗe da dunƙule hannunta A lokacin inka ganta zaka kasa gane inda yanayinta yake,shin baƙin ciki take ji kokuma tsoro da fargaba Ko tashin hankali ne? "Ke beenanxeer wai ko kunnuwanki sun daina aiki yadda ya kamata ne na dawo miki dasu daidai.?" Haka Moh Jiddoh ta sake rikirkita beenah cikin rawan jiki da dama yawanci a kawoma wani gulman wani kake cin ubanka jikinta baki ɗaya bari yake ta buɗi baki cikin sarƙewar numfashi ta furta. "Wllh da gaske ne nazo wucewa ta cikin balcony ɗin Oum jesrah naji tana zance da dukkan alamu ma waya take yine, shine fa na lafe naji tana cewa ƴargidan Mah data batace ta bayyana amma anan ɗin ba ita bace ƴartane ma wacce aka ɗaurama Boss Aure da ita wai Merrah!" Wani irin wulgar da beena ɗin moh tayi duk kuwa da cewar jikin tsufa gareta amma kai dama kallo ɗaya zaka mata kasan cewa irin tsofin najadun nan ne maƙirai. Wata sakakkar ijiyar zuciya ta sauƙe tana jin duniyar ma baki ɗaya na juya mata, kanta kuma na neman juyewa zuwa na masu ta6in hankali. Wayanta dake gefen Royal chiar ta ɗauka tana dannawa da alama wani ko wata take nema a wayar cikin gaggawa. "Hello Hussein? Maza ka bincikamin yanzu shin da gaskene matar da aka aurama Aboul-maleek aure da ita ƴar Easherh ta bayyana kokuma watace ne daban?, ina son bayanai yanzu yanzu sannan ka tabbatar babu wanda ya zargeka don nasan halin haukarka idan ya motsa kana iya kwa6emin aiki" "To shikenan Moh yanzu kuwa zan bincika ɗin" "Idan har ya tabbata haka ne to da akwai gagarumar matsala! don shirin da mukayi tsawon shekaru gaba ɗaya wargajewa zayyi,dan haka ka taka tsantsan ka ganomin komai, Amma ta wata hanyar da sauƙi domin idan harya tabbata Yarinyan itace, kuma ita aka aurama wannan shegen kaga kenan babu Aure tsakanin su, tunda da uwar yarinyar dashi tantirin uba ɗaya suke." Daga tacen Hussein ɗin yaja ijiyar zuciya hankalinsa na ɗan dawowa jikinsa sai kuma ya furta. "Wai to garin ya haka ta faru a bazata taya ma zakice haka duk shirin da mukayi na 6atar da Ita a duniya saida ta dawo? mtswwww aikin banza nikam ba samm ban yarda ba wllh moh" "Karka yarda dan mataccen ubanka! Nace karka yarda hussein a kana kallon yadda abubuwan dai suke kwa6e mana a cikin ƙaramin loƙutan nan" Kitttttt ta datse kiran tana wani irin runtse ido tareda jijjiga kai Kai tsaye Center table ɗin tsakiyar ɗakin ta fasa raga raga tana kuma tsaye, zuciyarta na neman faso ƙirjinta tabbas ta yarda sai yanzun abubuwan da suka faru a wancen ranar komai ya dawo mata a kuma ranar ne ita yarinyan ai tazo, kana a kuma ranan tayi poisoning na me martaba. "Wllh bazan yarda komai ya kwa6e min da wuri haka ba! Meyasa za'ayimin haka? duk Uban tsawon waɗannan shekarun dana ɗauka kenan a banza wllh bazan ta6a yarda nayi faɗuwar baƙar tasaba dole ki mutu yau _Jaddern Ashaan_ Duk kece sanadiyar komai kene kika shigo cikin rayuwata kika 6atamin ita wllh na tsaneki Na tsaneki Keda zuriyarki tsanar daban ta6a ma kowa ba a duniya" Tana faɗin hakan ta miƙe ko kallon gabanta batayi babban burinta kawai taganta a gaban jaddern Ashaan ɗin. Taku take me kama da sassarfa idonta har bata gani sosae zuciyarta kamar zata faso ƙirjinta ta fito. Haka ta ringa shiga tana fita ta cikin wasu 6oyayyan hanyoyi wanda haka har saida takai kanta ga wani surƙuƙun bakin ɗaki me tsananin duhu sosae. Wanda dattin ƙura da yana baki ɗaya suka baibaye ɗakin, da hannuwanta tayi amfani wajen fara share gefe da gefen tsakiyar ɗakin, take wani wuri da aka masa alamar zEr0 ya bayyana. Numbobine tsoffi irin na da ɗin nan suka bayyana a jikin wannan wurin bayan ta danna wata jar alama, numbobin da suka daɗe da zama haddattu akanta ta shiga daddanawa, a take tsakar tilen moples ɗin yaja gefe da gefe saiga wani da ɗaɗɗen gini ya bayyana kai tsaye ta shige ginin cikin ƙarƙashin ƙasar. Wata azabar shi kansa ginin wani ginin ne a cikinsa haka ba tare da tsoro ko fargabar komai ba ya faɗa dakin ƙarshen. Bin bayanta yake cike da fargaba mai cunkushe da tsoro,ita kuma ko waigowa bayanta bata yi kawai tafiya ta ke cikin sassarfa ta ban mamaki wanda hakan yasa dole Mahboob fara haɗawa da sauri-sauri gudu-gudu dan ya cin mata amma ina sai ƙara sauri ta ke harta shige cikin wani surƙiƙin dogon gini. Kai tsaye cikin dogon ginin ta shige shima ya mara mata baya cikin sauri, yana shiga yaga ƙofa ta samu da kanta ta rufe gidan kai tsaye nan ta ke wani uban duhu ya mamaye gidan baki ɗaya tamkar wata yayi nisa, Nan take hankalinsa yayi mugun tashi domin ko tafin hannunsa bai iya gani tsabar duhun cikin duhun ɗakin. Kai tsaye inda Jaddern Ashaan take a ɗaɗɗaure ta nufa wani irin yankawa gabanta yayi ya faɗi zuciyarta na barazana wa gangar jikinta ta hanyar fasar kirjinta ta fito. Cikin wani mugun tashin hankali da ƙinƙinar da bata san tana da ita ba sai yau ta shiga faɗin. "Me me me za zan ga gani hah ha ka ni Hauwa'u?, komai ya gama ƙare min ɗin kenan dai ko kuwa yaya ya?, to kadai mutuwa tayi ta bushe ta zama wannan burbuɗin kasan?" Ta faɗi tana me wawurar kasan da ta ɗan turu wuri ɗaya. Wata walƙiya taga ta gitta idanunta da wani irin hasken daya kashe mata idanunta sai kuma taji kamar an buga mata wani, Sai kawai ta tafi luuuuuu tayi ƙasa a sumeeee........ To masha Allah ai shikenan saimu gimtse anan ba? Hhhhhhhhhhhh Kai wllh nama rasa ta inda zan fara da tamboyinku da kuma yawan sharshinku mutanena. Kawai dai muje zuwa game rabo za'a warware komai dashi. *AMMEY LAYLERH taku ce* *🦅 MIKIYA 🦅* _A wonderful world & Special anti terroRism squad_ ____________________ *MARYAM NASEER MIRRAH* ~AMMEY LAYLERH ✍️~ ✯ *~🌠 JAJIRTATTU WRITER'S ASS.... 💫~* BOOK Two…………………………񆬍✍ 11&12 ♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡ **☆✭ ★ You Are My Dream Come True _Meerah AK 😊🙃🥰😍_** _MADINAH_ A ɗan tsorace Ash ya janye wayar a kunnensa wanda har hakan ya sanya queen Lajja dake basa gyaran kumba dago da kanta tana me dubansa a nutse. "Lafiya Ashfuddern?" Queen lajja ta tambayi mijin nata, kansa ya ɗan jujjuya mata yana faɗin. "Kamar dai kunnuwa sun ɗan sami raunin jine wllh Lajja, amma kar6a muga ji abinda ake faɗa! Daga lambar Lele Razeerh ne" Itama jikinta na ɗan rawa ta amsa tana manna woyar da kunnenta tare da jin furucin da Oum ta sake maimaita mata itama. "Kunnenka be samu raunin jiba Rahul hakane abinda kaji kuma daidaine" Tsaye ya miƙe har jikinsa na ɗan rawa kaɗan bada yawa ba, "Bani phone na" Ya faɗi a hanzarce. Bashi tayi kai tsaye number'n Zayeet Ash kai tsaye yayi calking. "Ina buƙatar jet yanzu yanzu maza xuwa Kuwait Zayeet Ash!" "Ko lafiya kuwa Abana?" "Ba tambaya nace kamin ba aikin zakamin kona nemi woninka yamin?" "Afwan Ya abana yanzu kuwa an gama" Daga haka ya yanke wayan yana cewa lajja ta shirya yanzUn zasu tafi babu jirah. A take Zayeet Ash yayi magana da pilot ɗin dake driver'n nasu duk inda suke so yayi akan ya shirya tashi yanzu zuwa kuwait. Babu 6ata loƙaci kuwa ya nemi izinin tashi 7 na magrib ɗin, 7:30 jirginsu ya tashi daga madina zuwa kuwait, tafiyan bame tsaho bace cannnn hakan yasa 8:50 suka sauƙa a masarautar kuwait. Kai tsaye Mah dake a sume suka fara gani tun a daren wacce har yanzun bata farfaɗo ba. Ganin me girma sarki Ash a sallar asba ba ƙaramin kaɗa hantar cikin hussien yayi ba, amma sammm hakan be nuna ba ko'a fuskan shi saima gaisawa da sukai cikin mutan taka da tattako. Daga nan masauƙi suka sake komawa ita kuwa dama lajja tare ta kwana da yarinyanta. Wacce sai a sanyin asubar nan ta farka da wasu surutai wanda ba masu ma'ana ba, Da kan lajja take a sake mata alluran bacci domin kwakwalwanta ya sake samun relax yanda ta kamata. ★★★ Ak tun a daren ranan oum ta sanar dashi abinda ya faru wand har kawo kwanan yau be ta6a ganin matar nashi ba, kasancewar sa6ani suke samu kuma ko zaid Merreh bata taba haɗuwa dashi ba. Hakan kuwa yama Oum daɗi domin kakaf labarin abubuwan da suka ringa faruwa tsakanin AK da MEERAH saida fulani ta bata labari wanda hakan shine abinda gafi rinjayar hankalin me marta, ganin duk faɗin duniyar babu mahaluƙin daya taba fira dashi bare batun bayyana kansa wa al'umma, amma ta sanadiyarta ya magantu tun daga nan me marta yasa aka ringa bibiyar masa duk wani motsin Ak ɗin tare da Merrah. Bama iyaka labari kawai ake bashi ba daga karshe komai ake may video nasu har kuwa ranan data kusan faɗawa ƙasar benen nan, anan maganganun yarinyar da kamu kamanninta suka haska may wani muhimmin sirri da tarun abubuwan mamaki, tun daga nan ya fara neman duk wata hanya da zata sada shi da iyayen yarinyar. Saidai kuma kash a loƙacin daya bayyana sai yayi rashin sa'a don saura kwana uku bikinta ma a loƙacin, Harya fara shirin juyawa wani ƙaddarern lamari ya sake haskaka hasken daya fara kalla tattare da yarinyan Harkuwa hakan ya kaishi ga nasarar haɗa aurenta dana mara jin jikinsa. Wannan kaɗan kenan daga cikin abinda fulani ta yankama Oum ɗin. Ak kuwa cewa yayi yau zaiga ƙarshen fitsarar koma wace tada yarda harta amsa sunan matsayin matarsa. Hakan ya sanya kai tsaye ya nufi Sashen mahaifiyarsa duk da kuwa yasan cewarn babu kowa bangaren nata. Kai tsaye daga yasan bedroom na jesrah nan ɗin ya nufa. Fitowanta a wanka kenan domin tashinta kenan alluran bacci itama oum tasa aka mata,sai yanxun take farkawa hakan yasa tana tashi ta fara da wanka don tana son jinta Fresh off kafin ta zauna nazartan komai tunda kuwa xuw yanzun tasan ba mafarki bane ba kuma cikin gushewar hankali take ba. Rigar wankane sanye a jikinta blue colour iyaka cinyanta sai farin towel data naɗe kanta a ciki. Wani mini kuma riƙe a hannunta tana tsane ruwan dake ɗiga daga fuskanta zuwa jikinta. Fararen santala santalan cinyoyinta tar dasu kamar wacce ake wankesu kullum da madara da zuma sai wani colour'n glowing suke. Sammm ita ba ma'abociyan son irin waɗan nan ƙananun kayan bace amma kuma tunda tazo ƙasar dole bata da za6in daya wuce hakan tunda bata isa ɗaura zani ta shiga wonka ba, yoma ina yake babu dama zani ɗayane kakaf kayan kuma tunda jesra daga dashi take amfani idan zatai wanka ta hanata sanyawa amma taƙi. Haka tanaji tana kallo ta ɗauke mata duka zanin harma da rigan akan hakan kuwa har ƙaranta takai wurin oum Amma ta bata haƙuri tace taci gaba da amfani da showel ɗin da kuma bathrobe dele haka take dannewa tayi amfanin dasu ba don taso ba. Towel ɗin dake ɗaure saman kanta ta ware tana kaɗa kanta tare dayin hajijiya domin idan ba jesra bace a room ɗin bata wani amfani da na'urar busar da gashin kai, tafi gane ta naɗo abinta a showel kana ta karkaɗe abinta ta taje shi tas. Sake baza gashin kan tayi tare da ɗagowa haɗi da ɗan turo baki gaba haɗi da faɗin "Jes kin gama dan....... Maganan tane ya maƙale a maƙoshinta haɗi da wani irin zaro manyan idonta masu kalan madara da kuma na ƴan mayen nan. "Ya rabbi.! Ɗan dabar can dai anan?" Harshen meerah da zuciyarta ke bugawa da sauri-sauri ya suɓuce wajen faɗa batare data shirya hakan ba. Aida wani irin tsalle ta buga sai gata tsaƙiyar bed tare da toshe kunnuwanta da hannayenta tana kurma uban wani ihu. "Na shiga uku Ni! Maryam, Innalillahi yanzu kai nan ɗin ma saida ka biyoni ko tsoron Allah bakaji?. Ka sani yanzun ni killatacciya na haramta da duk wata haɗawa dakai A yanxun haka ina amsa sunan matar Aur........ "Keeeeeeeeeee!!!" Ya daka mata wata kafurar tsawar data sanyata ƙamewa, "Ke mahaukaciyan inace hala? Kinyi ƙanƙanta dana bibiyi tatsitsiyar yarinya irinki nevermine har gaban abada" Duk da cewar a tsorace take kuma kanta a rufe yake da duka tafukan hannuwanta amma hakan be hanata murguɗa masa baki ba tare da furta. "To nidai ko miye na haɗaka da girman Allah ka fice a gidan nan baki ɗaya kaga nan gidan sarautane ba kamar nigeria bane daka saba dabanci wllh idan Mijina ya ganka zai iya halakaka! Tunda naji kowa na gidan tsoron shi yake ance ɗan zafin kaine wllh tsaf zaisa bindiga ya harb...... "Keeeeeeeeee!" Ya sake sakar mata wata tsawar yan faɗin "Allah ya kiyashe na harbe wani saboda mace macen ma ke irinki marar aji" "Wllh zanyi maka ihun ɗan iska tunda ba zaka fita ata arziƙi ba" "Uhumm Aha bara to na matso yadda zakifiyin me dalili ihun da kuma lasisi ganin dai da gaske gadan gadan nufo tan yake ya sanyata miƙewa a guje tayi hanyar data fito wata bathroom. Taku ɗaya tayi ana biyun taji ya ɗamki tsintsiyar hannunta, "wayyo Allah na wayyo Oum kina ina kizo wani ya shigo har cikin gida zai keta min haddi!" Wani mugun bugu ya kaima bakinta a take gefen lips nata yaɗan fashe ba da yawa ba kaɗan, "Idan kuma nine mijin sai kiyi yaya kuma?" Tuf ta tofar da miyau wanda jini ya ɗan biyo kaɗan "Allah ya rufa asiri ma ɗan daba irinki yazama mijina, kasani nan ɗin gidan mutumcine da masu mutumci kuma ka sakarmin jiki domin jikina me darajane me tsadane ba kowanne datti da ƙazamin jiki ne ke haɗa nasa da nawa ba na bayama ban yafe ba wllh" "Sai kuma Akayi katari _ABDOUL-MALEEK HASSAN EMAAR's nine nan a matsayin mijin naki! Idan har baki haɗiyi zuciya a daren yau kin mutu ba ke ɗin baki cika babbar mara kunya ba kuma naki _ZAFIN KAN_ kaɗan bame yawa bane" "Allah ya rufa asiri wllh dana zauna da ɗan ta'adda marar kishin ƙasar sa kalanka kara na haɗiya zuciyan na mutu tirrrrrr da mugun fata" Tana faɗin haka ta yanka masa cizon da yazo may a bazata wanda hakan shine ya bata daman guduwa tana Mirza ma bathroom ɗin Key. Numfashi ta shiga sauƙewa a hankali tanajin yadda zuciyanta ke bugawa, "Mugu! Azzalumi!!" Ta faɗi tana durƙushewa a wurin wani abu me zafi da narka Zuciya na dunƙule mata wuri guda. Cikin muryan kukan taci gaba da faɗin "What do you want?,why did you bring me here?, leave me I can't Meerah yanzu ni ba merrah ɗin da ka sani bace ada ni matan wani ce sunan matar aure nake amsawa azzalumi ɗan daba me satar mutane I hate you." Ashe ma bata sani ba ita kaɗai take abinta don tuni yabar bangaren ma baki ɗaya. Da kyar ta iya fitowa a bathroom ɗin tana jin yadda zuciyanta yake a cinkushe, Sallah ta gabatar anan idda take bacci me nauyi yayi awon gaba da ita duk wainar da ake toyawa kuwa bata sani ba har zuwa washe garin ranar. Da misalin biyu da rabi na rana baki ɗaya duk wanda yake da kusanci da waccen maganar sun gama kammala a babban palon Mah, Harda Sarki Hassan Al-hassan kasancewar jikinsa da sauƙi sosae taron zayeet ash ya buɗe musu da adda'a kafin Sarki Hassan ya furta, "Alhamdulillah Ahar kullum Allah shine abinda godiya me bayarwa da kar6ewa a sa'ilin da yaso!, Ayau ma shine ya sake haskaka mana wani hasken da muka jima da rasashi ta hanyar disashewar daya mana ya bace mana battt! Amma kuma cikin ikonsa da buyawarsa da kuɗirarsa ya bayyana hasken da muka jima da fidda rai da wannan Hasken kwasan kuma da yaso a rana guda, a wuni guda ya haskaka mana shi kansa asalin wannan hasken wato ya bayyana mana ƴarmu da muka jima da cire tsammani daga gareta wato Eash....... "Be kuwa bayyana muku ba wllh" Suka jiyo muryan moh jiddoh tamkar wacce aka wullo daga sama. "Idan har ina numfashi hakan bame yiyuwa bane! Kuma idan harda gaske ne yarinyar itace wacce aka ɗaurama aure da wannan tantirin kenan babu Aure a tsakaninsu kenan?, tunda uwarta yayar Abdoul-maleek ce" "Ba yayarsa bace" Nusassiyar muryan Sarki ash ya daki duka kunnuwansu tare da ratsa tsakiyar ƙirjin kowa. Gaba ɗaya kallo ya koma kansa ciki kuwa harta ita ƴar tijarar wacce dakyar mahboob ya samu ya cetota daga wannan shegen ginin ƙasar. "Kwarai kuwa ba yayarsa bace hasalima basa da wata alaƙa saita musulinci!" Cikin muryan nan da yake fita da kaushi kaushi da kuma hargagi ta furta "To saika mana ƙarin bayani tunda daduk kan alamu daga sama ta faɗo ba haifarta akai ba" Moh jiddoh ta faɗi tana wani harare hararenta. "_EASHERH ASH MAYESH_ , Ita ɗin cikakkiyar ƴata ce ta sunna kuma ƴar Auta ta" "Rainin hankali taya ƴar da na ni ce mutum ta farko na fara amsarta da hannuwana Loƙacin da Razeenerh ta haifeta yanxu kuma don son cika wani mugun nufi kace ba ƴarta bace?, to wllh inma auren kuke son halastawa to kuwa tabbas haramtaccene" "Moh Easherh kwarai ba ƴar dana haifa bace ƴar Ash ce" Wani mugun kallo ta data cillama Hassan ne ya sanya shi shanye maganarsa. "Uhummm tell me ina jiran ka sanar dani ta yadda aka haihu a ragaya" "Ganin a waccen loƙacin MATATA RAZEENERH bata haihu ba har shekaru biyar da aurenmu ne ya sanya sarki ash ƙirana ya sanar danj cewar, Idan har queen lajja ta haihu mahaifiya ga Razeenerh kenen ya bamu duk abinda ta haifa halak malak. amma karna sabarwa ma kowa tun kuma daga loƙacin Zeenerh ta koma can madina da zama da nufin tana laulayi me zafine moh idan baki manta ba a loƙacin haka na sanar dake?" Ya faɗi yana kallar moh ɗin kanta ta gyaɗa mishi alaman ehhhhh ta tuna da hakan, ci gaba yayi da faɗin. "Bata tashi dawowa ba sai a daren ranar da queen lajja ta haifi Autarta mace wacce suma haihuwar taso musu a bazata. A kuma daren naje nazo da zeenerh sai tayi kamar a masarautar ta haihu sai mukayi amfani da hakan gashi kuma dama babyn kamanninta ɗaya da Razeenerh kasancewar uwa ɗaya uba ɗaya ba ƙarya ba. a haka tayi rainon babynta saidai tarin wani abin mamakin sammm babyn taki amsan mama a wurin Razeenerh dole muka renata da madara har takai yaye ba tare da kowa ya fuskanci komai ba. A haka har takai shekaru takwas kwasam kuwa dare ɗaya rana ɗaya sama ƙasa muka Nemi Easherh muka rasa, wanda wannan shine tushen komai har bayan wasu shekaru tun muna san ran wata rana zamu ganta har muka haƙura muka fawwalama Allah komai. A haka mukaci gaba da zaman mu ba tare da zeenerh tayi ko 6atan wata bane, ganin hakan ya santa cemin nayi wani auren ko allah zai bani haihuwar, haka har auri Yasmine wato mahaifiyar Adeenerh abin mamaki ko wata biyu bata cika ba ciki ya bayyana a wurinta wanda kuma wata ƙudirar na allah saiga itama Razeenerh'nan da nata cikin. Kusan loƙaci ɗaya suka haihu fikonsu kwana biyar a tsakani, A kuma ranar da zeenerh ta haifi ɗanta namiji a kuma ranar Yasmine ta rasu. Bayan ta faɗamin wasu maganganu masu girma da nauyi. Rasuwanta babu daɗewa sarkin kano na nigeria ya bani auren ƴarsa wacce ada naso bijerama hakan saida zeenerh ta tunasar dani kana na amince,cikin ikon Allah kallon farko nama maryam naji soyayyarta tsantsa a zuciyana. Ashe Allah ya soni da rahamarsane da naso bijire masa ashe itace cikon mahaɗin garkuwan haskena. Bikinmu babu dadewa sai gata da ciki wacce ansha gwagwarmaya ba laifi baga Moh ba ba kuma ga matar biyunina ba matar hussein kenan domin kiri² suka nutsa tsanarta a fili babu ko kara. Daga inda ta haifi ƴan biyun ƴaƴanta duka maza wata _ABDOUL-MALEEK_ da kuma _ZAID_ Daga nan mabuɗin wasan ya soma har kawo kwanan yau kuwa!!!" A fusace ta miƙe tana furta "lallai na yarda gyaɗa mayaudariyace tunda akayita da kwanso amma ba komai ko anan A-Hassanu ka nuna min ban isa dakai ba na haifekane ban haifi halinka ba" Fuuuuuuuuuuu ta fice tana barin ɗakin domin wasan ai bezo karshe ba dole saita cika burinta kota kuwa shine ƙarshen numfashinta. Daga nan suka sake tattaunawa a tsakaninsu maganganu masu sarƙaƙiya kana daga nan xuwa gobe insha Allah zasu wuce nigiria don ganin cikon miradinsu su duka wato _ANNENMU_ kenan. Da da meerah za'a tafi amma Oum tace su barta suje saisu zo da annen, dake ma har yanzu babu wanda yasan da maganar ko jalal Ash be sani ba so suke sai komai ya kammala kana su bayyanama duniya. Drecly da sarkin kano sukayi maganar kuma dama acan zasu fara sauƙa. 7:50am jirginsu ya lula nigeria kwarya kwaryar liyafa aka haɗa masu a fadar kano kasancewar yau babban sarkine a kasarmu wato sarkin madina da kansa ba aike ba, ƙara kwana sukayi sai a washe garin ranar agains suka sake bin jirgi zuwa lagos kai tsaye kuma sarkin kano yayi magana da Malam Abdullahi gwani tun a daren jiyan. Da misalin sha ɗaya da rabi jirginsu yayi dirar Mikiya a garin lagos nan ma a gidan gwamnan lagos suka sauƙa wasu shegun manyan motoci kusan guda talatin aka shirya wanda duk na rakiyan me girma Ash Mayesh ɗin MADINA ne. A wani irin tsare aka shiryama fitan motocin kansu iri guda ne kasancewar duk wanda yake da labarin sarautar madina yasan cewar basa fita a mabanbanta motoci ko kuwa sunkai ɗari ne ko. Gaba ɗaya motocin Rolls R Rayce ne bugun 2024/2025 Blue black masu ting glass ga wani irin ƙawatan da aka ma motocin da ado irin na zaratan manyan sarakuna, Ko wacce bayan mota tana ɗauke da tambarin _ASH MAYESH_ ne wanda duk a iyaka daren jiya aka shirya hakan. Kwara ɗayace fara wacce ta kasance bullet proof ce, Duk inda suka gimla sai kaga anabinsu da video kasancewar labarin sarautar madina ba boyayya bace.tuni matasa ƴan zaman banza watk media trend suka fara baza video'n tare da ɗan short rubutu. _kome ya kawo Me girma sarkin madina sarki Ash mayesh zuwa nigeria me girmane don haka I'm waiting_ A jiraye suke dajin kome ke faruwa da abinda ya kawo shi ɗin. Tunfa daga farkon layin har zuwa ƙarshen baka isa ganin iyaka motocin ba, don kuwa bama masu lissafuwa bane dama jama'ar anguwa kuwa harma da wasu anguwannin sun fito dan ganema idonsu dill da dill. Duk kuwa da kasancewar birnine babu ruwan wani da wani to amma wannan batu ake na zaratan sarakuna wanda sukayi zarra sukayi fice a bangaren sarauta. Ganin inda motocin suka fakane yafi jan hankalin jama'a fiye da baya. A cikin masu leƙe kuwa harma da fitowa harda matan gidan. Amma banda Anne su kuwa sunce baza'ayi babu suna ko iyaka motar suka kalla wata rana sun bada labari suce sun taba ganin motocimsa. Saidai me? Tsaiwar da motocin sukayine a gaban ƙofar gidansu suma yaja hankalinsu. Wannan farar motan ita kaɗaice aka shiga da ita har bakin bishiyar settline ɗin dake ta gaban gidan. Wasu zaratan larabawan hadima maine suka kewaye motan tare da fara wata kalan busar sarewa wanda jin wannan busar ne ya sanya Anne tsayawa chakkk domin jinin jikinta taji ya ɗauka wani kalon tsuma tamkar irin wanda yayi kewar wani gi6i daga cikin rayuwarsa loƙaci guda kuma ya samu ko ya gani ko ji haka jikinta ya ɗauka tsuman. Cikin harshen labarci suke kirara wa sarkinsu su kuma fadawan kano na fassara musu, Malam Abdullahi gwani da kanshine ya buɗewa ma sarki Ash mayesh motan. Kyawawan fararen sawayensa da duk tsufa besa sun sanja bane ya fara zirowa cikin wasu shegun almurun bakaken halp cover irin sarakunan nan. Shine ya masa gajora har zuwa babban palon Anne domin yace baya da buƙatar ko ina muhallin Autarsa anan yake da buƙatar ganawa da yarinyansa. Cikin sauri sauran matan suka tari malam Abdullahi suna cewa ya haka duk sauran sassan gidan beyi masa ba sai a sashen Annen kawai zaikai baƙo me girma irin wannan?. "Babu inda mahaifi yafi dacewa da ya gana da ɗiyarsa inda ya wuce ɗakinta!" Wani mugun zabira sukai su duka biyun suna ja da baya tare da faɗin. "Ahhh Rainin hankali dai duk ƙasar nigeria bata isheku wasan kwaikwayon ba saikun haɗa da sarki me girma irin wannnan dan zubar masa da mutumcinsa kome?" Wani kalan yunƙurowa fadawan kano sukay dake sune masu jin duk abinda suke faɗan. muryan da sukaji ya dakatar da sune ya sanya su juyowa su kalli wurin, Ai da wani mugun bala'in gudu sukaja baya suna sandarewa. Don wani mugu mugun kaman..... . _To ai shikenan mu gimtse kawai nima bansan ko miye ba suka hango ɗin_ *BY AMMEY LAYLERH* _MIKIYA_ *🦅 MIKIYA 🦅* _A wonderful world & Special anti terroRism squad_ ____________________ *MARYAM NASEER MIRRAH* ~AMMEY LAYLERH ✍️~ ✯ *~🌠 JAJIRTATTU WRITER'S ASS.... 💫~* BOOK Two…………………………񆬍✍ 13&14 ♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡ **☆✭ ★ You Are My Dream Come True _Meerah AK_ Friendship 😊🙃🥰? ?_** Don wani kalan mugun kamannin Anne'n tsantsa da suka gani tattare da wannan kamilallar fuskan dattijon, basu sake rikicewa ba saida queen lajja dake bayan sarki Ash mayesh ta bayyana gabansu itama wanda kai tsaye kamannin Anne'nma duka natane. Ja da baya da baya suke jikinsu na rawan tsoro. Mah (Razeenerh) ce da taji shiru su basuy gaba ba basuyi baya bane ya sanyata leƙo da kanta don ita baki ɗayama tsoron gidan ne ya kamata don gani take taya ace ƴa mafi soyuwa a zukatan iyayensuce ke rayuwa anan wurin. Alhalin su suna can cikin daula da daula ƴarsu na nan na rayuwa a irin wurin nan. "Wllh yau munyi gamo ne Maman Abdallah nafsi nafsi" A haba sai aka shiga tsere tsakanin Matan biyu d0n ganin Mah ɗin ya ƙarasa juyar musu da kai baki ɗaya. Cikin anguwa kuwa kafin kace mene har tayi tafff da jama'a ƴan son ganin dill. Tun tana danne ƙoƙarin danne bugun da zuciyanta ke mata harta gaza dannewa, Raiha ce kwance a gefen Anne'n kasancewan yau weekend ne babu school. Sama take kalla busar sarewan da ake ci gaba dayi na sake bugar da ƙirjinta, Shin sai yaushe ne wai zata dena ire iren waɗan nan mafarkan masu cike da yaudara. don ba yau take ire iren mafarkan ba. Ba yau ba ba jiya ba, ƙofan da taji an taba ne ya sanya zuciyanta bugawa da ƙarfi Malam Abdullahi ne a gaba kafin Mah sai queen lajja me martabane ƙarshe. A nutsenta ta ɗago kanta don gastata kanta. Faɗawa da idonta yayine a cikin wata me balain kama da itane ya sanya jinin jikinta tsinkewa. Tafiya take hannunta yana nuna Anne wasu hawaye na ambaliyan ruwa a saman kyakkyawan fuskanta. "Ke ke kece DIDINA? Lajja wllh Easher'nmu ce wllh itane duk inda jininmu yake baya iya buya don a tafashe yake ba'a daskare yake ba! Har abada jinin Ash ba tauyayye bane ko wacce magudana ta jikinmu tafasa yake jinin mu a tafashe yake Ya abana" Haka Mah ta shiga faɗi tana kuma ƙara kusanta kanta ga Anne, hannu takai da niyar taba Anne'n ai kuwa taja da baya tare da ƙarema ma mah kallo tun daga kan suturar dake jikinta har zuwa ƙarshe. "A ahhh kada hannunki yayi yunƙurin ta6a wannan jikin, gudun kada ki bata naki jikin" "Ka gani ko Abaah ai dama na faɗa ma duk inda jinin Lajja da Ash yake baya taba buya har gaban abada wllh Easher ce itace itace itac......... Sai kuma luuuuuu tayi baya da sauri Raiha ta kwalla ƙara don idonta a kulle suke tin arbar da tayi dasu mah ɗin, ita a zaton tama gamo ne tayi buɗe idonta kuma daidai da faɗuwan da mah ta tafi zatayi. Kafin kowa a cikinsu yayi wani yunƙuri tuni Anneh takai gwiwowinta ƙass mah ɗin ta zube a jikinta,wasu hawayen ta bata san kona miye ba na saƙƙo mata. Da sauri Malam Abdullahi ya juya da niyar fita. "Ina ka nufa yanzun?" Muryan Ash ya katse shi daga shirin fitan da yay niya. "Tana da buƙatan ganin doctor ne" "Ba buƙatan hakan" kai tsaye queen lajja ya kalla tare da furta ki bata taimakon gaggawa" Ko kafin ya rufe bakinsa harta isa garesu ★★★ *KUWAIT* _drems ''Aslm!'' Umaymah ta gajarta sallaman tana tsaye daga bakin parlour'n tana kallon Moh Jiddoh dake zaune akan prey mad, Ahankali moh ɗin ta juyo ta kalleta ko second batayi ba ta ɗauke kanta, zama tayi gefen kujerar da Moh ɗin take Zaune tana ajiye wayarta a kusa da ita tace ''mun kwana lfy Jiddo?" Banza Moh ɗin tamata duk da tajita kuma in da sabo yaci ta saba da halin Jiddon dan mace ce ita mai jin kai har yaranta yiwa take waima a haka ƙaunar umayma'n take. Ringing da wayar moh ɗin ta fara ne yasa ta kalleta miƙewa tayi taje gun dressing mirror ɗin ta ɗauko mata Asaad ne me ƙiran wanda t take kira Autan ta dake England miƙa mata wayan tayi ta gagaya tana zama tare da ɗaukar tata wayar whatsApp ta shiga tana duba messages kallon message ɗin data turama Autarta yasmine tun friday da dare ta kalla, yanzun madai ganan alaman kore alamun har duba message ɗin tati kenan. Amma ta ƙi bata amsa _Hii Yesmeern lafiyan?_ Ta sake tura mata kuma yayi two tick kuma ta gan story ɗinta amma bata duba message ɗin nata ba sauƙa tayi tare da switch data'nta tayi ma baki ɗaya. Maganar da Moh tayi ne ya sanyata maida dukkan hankalinta thought bata ɗago kai ba akan Moh ɗin ''uhm Umaymah kenan ae shiyasa naso tun a wancan loƙacin naso mu gama da komai amma abun ya gagara gashi kuma a halin da ake ciki yanzun babu damar hakan!'' shiru Umaymah tayi na ƴan seconds da alama tana sauraren abunda Moh jiddoh ɗin ke faɗa mata ne ''Duk da ance shi icce tun yana ɗanyensa ake iya lanƙwashi, to amma ni duk da bushe ɗin zan iya lanƙwashin! Idanma ta kama da karyewa to kuwa karyashin zanyi don buƙatan kaina ya biya Moh'' duk da a karkace tayi maganar amma tasan inda maganar ta dosa. Murmushin gefen baki moh ta saki sai ta ɗago batare da nuna komai ba ta furta "Uhmmm dakyau ki kula sosae wajen lankwasar dai kar yazam mu ta sake kwabewa" Wani kallo ta jefa mata wanda kai tsaye jiddon ke ankare da ita, itama wani shegen murmushi tayi ita kaɗai tasan abinda take kwancewa da saƙawa. "Zan kula sosae karkj damu Jiddoh komai zai tafi a tsarinane tafiya a tsarina kuma baya nufin kwa6ewar aiki irin na wasu!" Kai tsaye jiddo tasan maganar nata ne kuma ta amsa kamar yadda umayman ke buƙata dama, "Aha Allah temaka na ce saimun sake haɗuwa". Dama kamar jira umayman take ko irin wacce take akan ƙayar nan haka ta miƙe zimbir tana barin parlou'rn a zuciyarta take faɗin. {Mayyar mata kawai kullum tana kan sallaya kamar wata mutuniyar kirki nan kuwa sai shegen iya ƙulla makirci da haɗa tuggun tsiya...} Tana tafe tana duba wayanta loƙaci bayan loƙaci kuma tana jan tsuka, kamar daga sama kuma sai ganin ƙiran yasmine tayi ya shigo wayanta. Saurin peak call in tayi gudun kada ta katse mata ƙira don tasan kaɗan ne daga cikin aikin Yasmine ɗin. Daga ta can bangaren cikin harshen larabci yasmine ta furta. "Hala akwai abinda yake tafiya ba daidai ba tunda naga saƙonninki harta email!ok?" "Loƙacin zamanki America ya ƙare yasmine don loƙacin fara farautane wannan! Amma ya kamata ki taho haka nan my be not my be forever kuma" "Kina nufin A maleek na Emaar's a yanxun haka Mommah?" "Yana a harma da tsarabnan wifey a tare dashi" Daga kwancen da take ta mike tsaye zimbir tare da faɗin "Ma me? Kamar fa mata naji kin ambata mom a taya A maleek zaiyi min haka? Shikenan kitsimayi zuwana Later" Daga haka ta datse ƙiran tare da dafe kanta da taji loƙaci guda ya balain sara mata. "A wannan karon dole ka faɗa hannuna Abdoul-Maleek Emaar's ko kaki ko kaso mata ne bisa kanka wanda ake mana laƙabi da gangar shaiɗan" _Amma wait! Nidai nace babu ni Ammey Laylerh tare da duk me karanta littafin Mikiya Uhummmmm_ ★★★ _Some late_ Karon dataci da wani abu kamar gini ne yasata saurin ɗagowa tana yin one step back hannunta dafe da hancinta data buge tare da forehead ɗinta amma hancin yafi mata azaba A hankali ta soma ɗagowa dan son tabbatarma kanta wanda ke tsayen saboda wannan unique ƙamshin da bata ta6a jinsa jikin kowa ba sai jikinsa ɗin. Kallon kallo sukewa juna ita dashi kasancewar sa mutum mai tsayi sosai kuma dai kunsan tsawon mace dana namiji yanda suke hakan yasa ta koma wata ƴar karama. ''Halan kai makaho ne?'' da ƙarfi tayi maganar dan ganin yanda yawani mata tsaye a gaba tamkar wani bijimin sa. Idan inda suke tsaye yayi magana to shima Ak yayi, jin yaƙi ko tanka mata ne ya sanyata sake faɗin ''Malam nace baka gani ne? kokuwa iccen daka buge baiji maka ciwo ba?'' ta faɗa tana hayayyaƙo may ta buɗe baki kenan da niyar sake magana muryan Jesrah ta dake tahowa ta katseta. Cikin shegen rainin hankali ya dubi jesrah tare da faɗin''dalla malama hold it na ce miye wannan aka kawowa mutane gida'' da sauri jesrah ta duba ak ɗin tare da faɗin ''Akie Merrah ne fa'' Wani kalan yamutsa fuska yayi tare da furta''miye wani Merrah kuma?'' yanda Yake yatsina fuska kamar yaga kashi ne sake hasala Meerah ɗin itama. ''Akiey Matarkane fa wanda aka ɗaura ma aure da ita already tuni'' wani irin shegen murmushi yayi yana yuja kai ya tabe baki irin anzo wajen Nan. ''Au cemin zakiy kaskar data maƙale tace saini, wacce tabi duk wani lungo da saƙo don ganin ta shigo rayuwana. Fine amma bara na tuna miki wani abinda basu faɗamiki ba nan gidan ba kowane mara aji ko jani talau ne yake iya shiga ba bar ganin kin samu shigowa fitan ma ba wahalan zaiyi ba kamar shigowanki EMAAR's...... Ɗagowa Merrah tayi a karo na farko tunda suke tsayen ta kalleshi straight in the eye. Tare da furta. "Who are you? How dere you?" Ta faɗi in a low dangerous voice, kafin taci gaba da faɗin. "Saidai gidan ma ai beyi kama dana mutane tunda ba'a daidai ɗinsa yake ba, Kuma a kallon farko ma gidan beyi kama da gidan da mutane ke rayuwa a cikinsaba baki ɗaya duhu da duhuwa ne kewaye da durƙushashshen kangon ginin daya yake a baybay" Da wani kalan kallo ya bita me kama dana rainin hankalin nan. "Idan ma dalilin wani abu yasa kika nace saikin shigo gidan nan toh ki sani bakida muhalli a yanzu dan the house is full with children's no more room for you'' Yana faɗin hakan ya wuce abinsa bayan ya mata wanna shegiyar alaman datafi tsana fiye da komai daga gareshi. "Babu wanda besan halin Akiey ba so inaga hakan ba abinda damuwa bane dear!" Taji muryan jesrah tana jan hannunta lips nata taɗan ciza bada yawa ba tana bin bayan jesran don dama wurin oum suka nufa data aiko ƙiranta. Oum ɗin ta tarar zaune tare da jesrah wacce ta labartama oum ɗin komai daya faru. Cikin ƙarfin halin Oum tace "$higo man Meerah kinzo kin tsaya a Kofa? Zonan kusa dani kinji ta faɗa tare da nuna mata gefen da take zaune,murmushi ta yi tare da karaso ta zauna kusa da itah kamar yadda oum ɗin ta buƙata ta sunkuyar da kanta ƙasa tare da faɗin. "Oum good afternoon" Murmushi Oum ta saki tare da da amsata da "Lafiya Alhamdulillah baki biyo bayan iyayenki nema zance ns ko kakanni nema" Ɗan murmushi kawai meerah ta saki tana jinta a takure da zaman da sukeyi ɗin, dan har yanzu ta gaza sakin jikinta da oum don sosai take kunyar matan yanzun ma jinta take kamar ta gudu haka taji aranta. "Jesrah kuje ku gaida mutanen cikin gidan" "Tomm Oummuh" Jesran ta faɗi ko kafin ta miƙe kuwa tuni zaram har meerah ta rigata miƙewarma, kai tsaye bangaren Umaymah jesrah ta fara raka Meerah ɗin. da wannan shegen makircin nata da zagon ƙasa ta tar6esu faran² Allah'n baka. Basu wani jima ba sosae suka mata sallama wasu manyan arabian jallabiya tare da Alkyabba da turaruka masu tsada sosae ta haɗa meerah dasu. Ko kallon kayan batai ba jesra ne ta amsa tana mata godiya. Daga nan bangaren Moh jiddoh suka yi a loƙacin tana zaune ne akan caution tayi crossing ƙafafunta tana karkaɗasu idanunta a lumshe ita kaɗai tana aikin saƙawa da kwancewa. Wani kalan buɗe idonta tayi tare da juyowa zuwa wani mummunar faduwa gaban moh jiddoh yayi zuciyarta ya shiga harbawa da sauri-sauri idanu ta rufe ganin wani irin haske mai bala'in karfi ta cikin idanun meerah ɗin batayi auni ba taji muryarta na cewa "Innalillah wa'inna ilaihir raji'un meke shirin faruwa dani ne haka ni jiddoh yau na shiga uku!" Da sauri jesrah ta fita a ɗakin tana cema Meerah tana ɗan zuwa don wayan da aka ƙirata. Wata nannauyar ijiyar zuciya Moh ta sauƙe tare da furta "wllh shegiyar yarinyar nan tsoro ta bani kodan jinin mayuce masu shegen ƙarfi jinin tsiya tirrr dai wllh har abada ba'a taba sarki biyu a guri ɗaya" tayi maganan tare da buɗe idonta ba kuwa su faɗa ko ina ba sai cikin na meerah. Baki ta buɗe mata tare da daƙune fuskanta sai kuma gata zaram akan jiddon. "Da kina yarinya bakiy karatu bane? Cokali ɗaya na nonon sa yafi daro ɗaya na nonon jaki, uhmmmm dama saida nai tantamar ba'aje makaranta ba. duk aukin jakuna ba zasu taba kama ƙafar doki a gudu ba. Kuma har abada zakara shi kaɗaine sarki Moh ɗinmu ta ƴan gayu" Ta waske abinta tana kamar gyara mata rufin hulan kanta tayi ganin shigowar jesrah. Saƙeƙe haka moh tayi tana me bin meerah da ido kawai fakar idon jesran tayi tare da ƙyafta mata ido ɗaya da kashewa. "Ina ganin mutafi haka nan ko dear?" "Ehhhhh hakan ma yayi. Moh sai haɗuwa ta gaba yanzu ta wuce sauri muke ki kwana cikin sauƙin zuciya Allah kuma yaja da ranki kisha kallo my kakas" (Yau naga yadda ake bariki ni mai jiddah, to kodai akwai abinda yake ba daidai ba ko yake a baybay bana da masaniyar hakan kuma?) Ta ayyana a zuciyarta tana jinjina ƙarfin halin yarinyar, {kai ina wllh ma tana da aljanu yarin yarnan} ta sake maimaitawa tana faɗawa bedroom nata. Haka Moh ta kwana datunanin abunda ya faru tsakaninta da Meerah sosai abun ya tsaya mata a rai,tunda take bata ta6a ganin makaman cin haka ba a iya tsawon rayuwarta duk me hakan ke nufi?, ya zama dole ta shirya ma zuwan waɗan nan jerin abubuwane ma zata ce ko ƙaddarori ne ma oho da wanan tarin tunanin bacci ya ɗauketa. A ta bangaren meerah kwana tayi da tarin abubuwa maban banta wanda suka farun min dama wanda suke kan faruwan. Ruɗani,mamaki, al'ajabi sun taru sun hana Meerah runtsawa a wannan dare. Kanta ya gama kullewa dangane da abinda duk suka faru ɗazun tsakaninta da Moh da kuwa wannan Aljanin. Shin mutumin nan ɗan dabar ne da gaske? Kokuwa wani abu daban da bata sani ba. Babu abinda ke mata kaikawo a zuciya sai kalan yadda ya ringa yaba mata maganganu da kuma haɗuwarsu na jiya daya bita har ɗakin ta me hakan ke nufi kenan? Ita kam al'amarin wannan gida ya fara birkita mata lissafi tun a farkon shigarta komai ya gama bayyana kansa gareta. A lissafin ta dai Moh jiddoh itace uwar masu gidan to amma ta ya ya Akai ta kasance me fuska biyu. Abubuwa sosea ya hango tattare da matar baƙaƙe ba masu lissafuwa ba. Zuciyarta a ƙone take babu ko ɗigon rahama idan har lissafinta ya bata daidai Kenan 6atar da Annenta akayi a cikin wannan masarautar? A tunaninsu ita ƴar gidan ce kenan miye silar mutuwan matan me martaba ga biyu? Zancen daya faɗa a baybay ita tuni ta gama fayyace abinta filla filla tun a ranar. Kuma ita kaɗai tasan abinda taga ni ta kuma ɗaukarma kanta alƙawarin bibiyar kowa da kowa na wannan masarautar har zuwa kan dalilin da yay bacewar annenta. Kenan Anne ita bama ƴar nig bace Sarki Ash dai shine cikakken mahaifinta Allahu ahaad lallai Allah da girma yake. ? Sai wajajen ƙarfe biyun dare bacci yay ciki da ita cike da tarin wasu mafarkai masu ban tsoro. A hankali hasken rana ya bayyana a sararin samani. Wanda haka yayi dai-dai da farkawanta tare da bayyanan ciwon da taji maranta ya harba mata, ya mamaye duka har sassan jikinta da zuciyarta. Wani irin rumtse idonta tayi tare da tashi zaune cikin wani irin gigitaccen ciwon da ya mata dirarn farat ɗaya tace. "Sheehhhhhhh Wayyo! wayyo!! wayyo Allah Anne na ciwo zafi wayyo Raiha wayyo kowa da kowa na cikin duniyar ma baki ɗaya. Wayyooooo" Ta faɗi da ƙarfin daya farkan da jesrah a zabure don babu jimawa da komawansu bacci bayan sunyi sallar subhi. "Subhanallahi Aunty meerah mike faruwa?" ta tambayeta cikin muryan bacci tana mikewa tare da nufo wurinta, wani irin juyi haɗi da murƙususu meerah keyi wanda hakan kai tsaye ya sake firgitar da jesrah kai tsaye ta fita a dakin da gudunta domin sanarma da Oum. ★★.....★★★ A ta bangaren umaymah tun a daren jiya ta gama shirya komai na tarbar dolky'nta tun daga kan abincin da takeci har zuwa tsaftar sashen ma a yau ta kasance ta musamman duk da a kullum a tsaftace yake. An shirya kalolin abinci da ƙamshinsu ya gama cika ko'ina na sashen har maƙwaftan shashen ma ka iya jiyowa. Duk ata dalilin son ta farantama dolly'n. A mugun guje rantsatsiyar baka wulik ɗin lafiyayyar motar da dolly ke ciki ta tsaya gab da ƙofar shashen umaymah, cikin rawar jiki ɗaya daga cikin Hadiman ya buɗe mata motan, sauran kuwa tuni sun zube ƙasa kan gwiyawunsu kawunansu a ƙasa domin kai tsaye sun san dokar madame dolly'n DA'DAH. Tun a farkon shigowan motanta kuwa cikin Mention ɗin hadima suka dinga tsere don gujema haɗuwa da ita bare takai ga yi mata laifi. A ƙalla taja Sama da mintuna goma batafito ba duk da kasancewar an buɗe mata, sai da taga dama dan kanta sannan ta ziro ƙafarta fara tas dake a cikin ƙyaƙyƙyawan blue ɗin takalmi mai tsananin taushi da ɗaukar ido da zai iya birge duk wani mai kallo, Wanda yaci uban naɗi da igiyoyin dake jiki, kusan sakan biyar a tsakani sannan ta ƙara zuro ɗayar cike da ƙasaita. Tashin ƙamshin turarenta da takun sawayenta ya tabbatar ma duk wani rai mai numfashi ata bangaren isowarta. Wanda hakan kai tsaye ke sanya su rusuna kawunansu ƙass gudun haɗa ido da ita kayi laifi. Cikin wani shegen taku take wucesu hancinta ɗage a sama tana wani huhhurashi sama ita ga ƴar zafin kai. Wasu shegun ɗamammun riga da wando ne a jikinta na jeans iya ma'alwantarta kan nan naɗe cikin swear band me shegen kyau da tsaɗa, da wani irin maɗaukakin farin ciki umaymah dake zaune ta miƙe tana rungumar yarin yar nata. Kafin da hannu taima dukkan amintattun hadimanta dake zagaye da ita nunin su fice. Har rige-rigen bin ƙofar da zata kaisu falon farko dazai fiddasu ta ainahin ƙofar sashen nata suke. "I miss u my dolly'n Dada" Wani iska taja tare da jan numfashi ta fesar a hankali. Idanunta ta ɗan ƙankance da jinjina kanta tana sakin ɗan karamin murmushi domin Dada ɗinta da tafi kewa fiye da komai har ita kanta momman kuwa. Ita kuwa Umaymah da take jin duk wannan ranar tanajinta rana ta musamman ne a gareta, sakar mata kiss a goshinta haɗi da zaunar da ita tamkar bata baby. "Mommah Kina lafiya?". "A zahiri dai lafiya nake, amma a baɗini cike nake da tarin damur dake cinkushe a raina first" Umayman ta faɗi fuskanta na sauyawa daga yanayin farin cikin da take ciki zuwa kishiyarta. "Uhhm!" Yasmine ta faɗa da ɗan lumshe idanunta ta buɗe Still a lokaci guda. "Kai tsaye ki faɗin damuwar don nima yanzun haka a cikinta nake saidai jin wannan lamarin ya shafe wancan ɗin don shi serious bane kamar wannan ɗin" Kai tsaye ta ɗan tsaƙuri lamarin a ciki ta bata. Idanunta a lumshe suke buɗesu tayi tare da fesar da numfashi ba tare data bata amsan tambayar data mata ba ta furta. "DADA fa?". Tay maganar a fisge tamkar yinta ya zama tilas ne a gareta. "Yana mashel kotra" Wani kalan zaro idonta tayi wanda suke a bugu wanda kai tsaye inkai mai fashimtane a take zaka fahimci ba'a daidai suke ba. "Be dena zuwa Mashel kotra ba har yanzun kenan?" ???........... *BY AMMEY LAYLERH* *🦅 MIKIYA 🦅* _A wonderful world & Special anti terroRism squad_ ____________________ *MARYAM NASEER MIRRAH* ~AMMEY LAYLERH ✍️~ ✯ *~🌠 JAJIRTATTU WRITER'S ASS.... 💫~* BOOK Two…………………………񆬍✍ 15&16 _DEDICATED TO ALL WRITERS ALL OVER THE WORLD_ ♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡ **☆✭ ★ Hot Reletionship scene **☆✭ ★ Hot love **☆✭ ★ Romance scene **☆✭ ★ ❤️❤️❤️❤️❤️ "Ehhhhhhhhh" Ta bata amsan tambayan data mata tsaye ta miƙe ranta a bace har zata wuce sai kuma ta tsaya chakk tare da faɗin. "Wannan ɗin duk laifinki ne Mommah" Daga haka ta wuce side ɗinta sai ƙamshinta kawai data barma Mom ɗin nata itama tsayen ta miƙe tana me nufar nata side ɗin don ƙiran Hussein. Taƙira wayansa yafi sau cikin kwando amma yana Ring baya ɗauka haka ta hakura badon taso ba. Ko cikakken five minutes batai ma sai gata ta sake fito sanye cikin 3ter ɗin bakin wanda da bakar riga hannunta riƙe da car key sai uban glasses ɗin data rufe idonta dashi, kota kan mom dake mata magana akan ina zata je bata biba bare abincin da take mata tayi. Wata Mota ƙirar Mercedes Benz 2024/2025 ta ɗauka kota kan hadiman dake famar zube mata bata biba domin babban burinta takai ga inda Dadanta yake a yanxun. Gudu take sharawa tamkar ba mace ba cikin ƙanƙanin loƙaci sai gata takai cikin harabar wajen shakatawar. Don gudu tayi bana wasa ma tamkar motar zata tashi sama. A daidai table ɗin wasu mutane ta taka birki wani shegen birki. Suna zaune a gaban wani table su kusan biyar sai mace ɗaya. wanda samansa ke ɗauke da kwallaben giya dukkansu su biyar ɗi. su na sanye da kayane na shan iska. Cikin fushi haɗi da zafin zuciya ta banko motar ta buɗe loƙaci ɗaya ta fito da gangar jikinta tamkar wata kububuwa, basu an kara ba tasa ƙafa ta tashi table ɗin giyar nasu dukansu suka zube ƙasa . Ɗaya daga cikinsu ne ya ɗago kai don ganin isshashshen daya musu hakan, saurin faɗaɗa fuskansa yayi da murmushi wanda ba yaro bane ba, kallo ɗaya za ka yi masa ka gane zai iya bama shekaru 60 baya ya gama mallakar hankalin sa sai dai kashhh! wannan wajen girma yayi gardama ya kuma faɗi. Dan zungurin dada wannan mutumin yayi wanda ya ɗago kansa Cikin murya ta wanda yake cikin maye ya lumshe ido ya tare da sakin murmushin yaƙe "Dolly'n Dada! Sauƙar yaushe babu sanarwa babu komi kuma gashi ina hurin rihazal nefa na koyar rawa. Don wllh so nake nafi wancan ɗaya a cikin biyun iya rawa da waƙa. Kinga idan ban sami sarautar Emaar's ba zan tsira da waƙar kob...... Maƙale masa maganan yayi sakamakon , Cikin ƙarin baƙin ciki ta dakatar dashi shi Cikin fushi kamar zata wanka masa mari ta fara magana " Dada what's wrong with you are you out of your mind? na tabbata duka abubuwan da kuke aikatane yake bibiyanmj ɗaya bayan ɗaya kaico da zuwa danai ba'a ƴar sa'a ba I will...... "Yasmine!!!" Dadan ya faɗi a tsawace tamkar ba wanda ya gama magana cikin maye ba "muje gida" Ya faɗi kwalbar giyar dabe ƙarasa zubewa ba ta ɗauka tare da kwankwaɗeta a take. Wanda Dadan nata yabita da kwallon tashin hankali "yasmine kinsan abinda kika aikata kuwa wine giya giya fa kika sha?" "To maye don nasha ina kaima sha ka gama yanxun kuma dama shi sharri a ɗan aike nd duk inda yaje saiya dawo ma da amsarka don haka ka amshi wannan as matsayin amsar aikenka Dada" Wani kalan jar birki yayi ita kuwa ci gaba da takunta tayi ta shige cikin motan ta tare da bata wuta tana barin harabar wurin...... _NIGERIA_ *Lagos* Wani gwauron numfashi Mah ta kawo tare da ƙamƙame hannun Anne dake cikin nata cikin ƙasa da murya cann take faɗin. "Easherh ki yafe min ni yafe ma DIDI'NKI BODDO'NKI Komai daya faru ba laifinta bane. Hakan rubutaccen jarabawarmune tun daga rabbis samati karki yanke mana irin wannan hukuncin Easher'n Didi!" A hankali take zare hannuwanta ana mah ɗin. "EASH ASH MAYESH?" Taji dakakkiyar nusassiyar muryan dattijon ta ratsa har tsaƙiyar ƙirjinta. Bata da kwarin gwiwan bijirema zuciyarta ga abinda take shirin aikatawa. Don haka ta miƙe jikinta a matuƙar sanyaye ta isa har gaban Ash tare da kafe shi da idonta da nashi sakk ta gani kamar nata. "Shin wanne irin laifi na muku dana chanchanci wulaƙantarwarku har haka?, Ko makaho ya laluba tabbas yasan jinin dake gudana a nawa jinin nakane. Amma me yasa? Me yasa kuka aikata min haka shin ashe idan wani laifin na muku ban chanchanci da ku yafe min ba, na buɗi ido na ganni inda bansan ko wacece niba nayi kukan rashin wani ko wata dazan ƙira da nawa ko tawa ƴar uwa ko ɗan uwa na nesa kona kusa. Shin a rayuwa kunsan irin ƙalubalen rayuwar dana fuskanta a cikin wannan duniyar wannan jinin dake gudana a jikina an buɗi baki an ƙirashi da najasa haramtacce ma'ana har ƴar karuw..... "EASHERH ASH......." Queen lajja ta furta da ƙarfin daya sanya har na bakim palon toshe kunnuwansu. "Jinin AsH jinin AShaan Jinin lajja ake ƙira da jinin karuwa me yasa beyi zafi ba? Me yasa be tafasa? Me sa beyi aikinsa akan masu faɗawarsa don har gaban abada kinin AsH da Lajja Yafi ƙarfin a wulakanta yafi ƙarfin tozarci jininmu me zafi ne a tafashensa yake har abada ba'a taba ɗaga mana yatsa mu ƙyale! A in....... Shiru tayi sakamakon riƙo hannunta da ash yayi da ido ya mata alama da tayi shirun haka nan, Tattausan carpet ɗin da yanzu baffansu Raiha ya shimfiɗa musu suka zazzauna. Har zuwa loƙacin kuwa Anne kukan take a nutse lajja ta Janyowata tana ɗora kanta a kan ƙafafunta. Wata nannauyar ijiyar zuciya ta sauƙe loƙacin da taji hannun sarki Ash ya dafa saman kanta a karo na biyu masu hawahen suma sake balle mata wanda da gaza fahintar na tsananin daɗi ne ko akasin hakan. Da hannu Mah dake kwance kan ƙafafun Anne itama taya fito Raiha a nutse ga ƙaraso ga matar me tsananin kama da Annenta. Kwantar da ita tayi akan jikinta tana shafa gashin kanta da yake a tsefe. "Ƙawa bani labarin Ningeria" Mah ta faɗi cikin juyayyar hausanta da abin ma abin dariya. "Amma kafin nan miye sunanki?" Ta sake tambayarta ijiyar zuciya ta sauƙe tare da faɗin. "Mu biyu ne ƴaƴan Anne nida Didi Ita sunanta Maryam ni kuma Razeenerh amma tana ƙira na da Raiha ma'ana kebantacciya. ita kuma Didi ta tafa faɗa mana cewar kamar tanaji a jinin jikinta kamar ta taba rayuwa dame irin sunan haka nan" Wani irin sake rungume Raiha Mah tayi cikin jinjina iko irin na ubangiji kenan harda sunan lajja da nata Didinta ta sanyama ƴaƴanta. Duk kuwa da cewar ba duka bane ta gane abinda Raiha ɗin ta faɗi. "Allahu Ahaad! Allahu Ahaad!!Abaan lajja kuji wani ikon allah ko lallai jinin dake yawo a tsakankaninmu me ƙarfine" Wani tattausan murmushi Sarki Ash ya saki wanda yaja hankalin lajja itama ta saki nata murmushin. "Nifa kun gindayar dani gaba ɗaya kaina ya ɗauke wuta. Wai me ke faruwane ku sanar dani" Suka jiyo muryan hajiya umma da shigowarta kenan wanda daƙyar aka barta ta shigo don anguwar cike take maƙil da soldier's. Ta faɗi tana zama kusa da Anne hannunta anne ta matse a nata bappa da kansa ya mata bayanin komai nan itama ta shiga jinjina ikon Allah da karfin zatinsa. Nan Anne ta gabatarma dasu mah Hajj umma. mafi yawanci sarkin kano shike fassarar musu maganganun shi yasa firan nasu beyi tsaho sosae ba. Daga nan bappa yaje ya shigo da abokanan zaman Anne habawa zokaga yadda ake rarraba idanu tsakaninsu. Wannan fa shi ake da tsammaci abinda baka tsammata ba ashe ita ɗin ƴar sarautace jinin sarautace gaba da baya haba no wonder take da shegen kwarjinin tsiya da rashin ɗaukan no nonses. A kunyace suka gaida su sarki ash ɗin da zancen kurame don basu ma san mine zasuce tunda ba karatu me zurfi sukayi ba, a loƙacin kuma malam ke koya musu sukace sun wuce ajin a koya musu yanzu yanxun kuma ga ranar ajin yazo babu ajin. Kafin kace mene saiga labarin zuwan ash nigeria da dalilin zuwansa nata zama trend a media. Haba wa tuni duk wani me alaƙa da gidan malam abdullahi yayo maza ya garzayo, saidau wata sabuwa anguwar kanta waɗan nan soldier's ɗin sunyi block nata sunyi crossing motocinsu ta ko wanne shashe na anguwar. Saida sukayi sallan zuhr wanda zayeed ne yajasu kana suka koma wani shegen estate guda governor ya basu. wayyo allah zo kaga yadda masallacin yayi wani kalan cika a ranar har bakin anguwar sabida balaraben da ya jasu sallah. Kwanansu biyu suka fara shirin juyawa tare da Anne har dama hajj umma da Bappa don sunce a can ƙasar su zasu bada labarin yadda rayuwar annen ya kaya. Da da farko taso bijirewa amma kuma malam abdullahi ya bata kwarin gwiwan tafiyan kodan taje daga ƴan uwanta na jini ita taji tana da ƴan uwan da kuma dangi kamar kowa wannan shine mafarin komai. ♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡ Duk inda tura takai bango wannan shegun samudawan Ak ɗin sunƙi bayyana kansu haka kuma sunƙi bada wata ƙofar da za'a iya cimmusu. Don Tight security legency'n Ak ɗin will forever live in nigerians mind. Don he's a legend and a here. Kuma duk wannan abin yana faruwane tare da sa hannun Kamaal Rano da Ak ɗin ya damƙa komi a hannunsa. Haka har suka gama haukarsu tare da nemansa da akei ruwa a jallo, Shi kuwa bangaren salman abu kamar wasa saiga ƴar ƙaramar magana na neman zama babba don duk wata na belin ɗinsa a toshe yake wanda kai tsaye suma umarni suke amsa daga sama wanda kuma saman basu san waye ba daga ina yake. Tun Isa manu na boyar kansa harya bayyana don wannan videorizeeng ba ƙaramin bacin suna ya janyo mishi. Wanda har saida General A..K..K shugaban ƙasar ganzu ya magantu akan wannan maganar.A a nan fa suma hankalin su mom surry ya fara dawowa jikinsu don tun tana zaton itace ta musu ɗaurin talala sai take ashe suma su duka harda ita aka ma ɗaurin talalar baki ɗaya ga kullum surry cikin kuka da ƙorafi dake mata akan itafa lallai mijinta take da buƙata sakamakon abubuwan data kinsa mata. Iyaka wannan kaɗai kan tashi hankalinta matuƙa Momen salman kuwa abu ya haɗu ya haɗe mata goma da ishirin gashi tashi ɗaya ƴar aikinta zeey ta bace bata battt tayi batan dabo dade da no nata baya tafiya. Gashi yanzu isa manu shi kansa yana cikin tention yake na kulle masa yaro. Babu shiri Audu bashasha ya baro ƙasar india don dama ya gama warkewa tsoron aran gamarshi da Ak yake tsoro. yaga kuma komai ɗin na shirin sake kwabe musu, don kenan hakan ma salon wani yaƙin ne aka ballo musu wato da niya aka bar Isa manu aka garƙame masa ɗa yadda abin zaifi sukarsa gashi dai yana da duk wata dama saidai sammm damar taƙi samuwa a gareshi harda ma magoya bayansa. Lallai sai yanzun suke sake yarda kuɗi ba komai suke iya saya ba a duniya indai akace da adalci babu son kai to kuwa har abada gaskiyace gaba da ƙarya duk girmanta koda takai tekun maliya a yawa. Gashi daga ƙasar poland sai daga company'n (E) group sai ƙiranshi suke akan lallai idan salman bai je a cikin week ɗin nan zasu janye shere ɗin da suka sanya hannu. Shi kuwa ko karen haukane ya cijeshi bazai ta6a bari ya rasa hannun jari a (E) Group ɗin ba ganin yadda yanzun shi ake yayi duk wani sabbin news da zaka samu ana yin sane akan (E) Group companie's. Audu bashasha kuwa a daren ranar yama Nig dirarn mikiya don shima yana da nashi taskon tunda yaronsa Farouq har yau Ak ɗin be sake shiba yana a hannunsa. Kuma tunda Su Ak ɗin suka ɗauke shi kome kama da labarinsa basu kuma jiba bare gani ko a news. Iya tashin hankali Ak ya tashi hankulan mutanen nan fiye da zaton me tunani. Gashi kuma duk inda jami'ai suko so gasgata fitan Ak a ƙasan hakan ya gagara don Inspector kamaal Rano tsaye yake akan hakan. Don indasuka fuskanci cewan ak baya ƙasan shikenan komai ka iya faruwa komi muninsa kuwa. Don kuwa komai ahannunsa Ak yabar komai kuma kwatsam rana tsaka saiga tantirin zaid ya dawo nigeria a matsayin Ak wanda ko yaransa basu gane ba tunda su dai ba sanin ƴan biyu bane suka. Kuma dama ba yau ak ɗin ya saba musu haka ba don komai nashi zaid babu abinda be iya ba kuma babu lungo da saƙo da ak yake zuwa wanda shima be sani ba nan fa aiki ya sake daukan zafi. Don a iya shegen zaid wanda yafi ak ɗin rawan kai da kuma zafafa kansa akan abu tuni ya matsama waɗan can bayin Allah'n lamba akan komai nasu, Iyaka kamaal ne kawai yasan ba Ak ɗin bane sai kuwa Arms da suka dawo tare da shi sai Riyya itama wanda kallo ɗaya zaid ya mata ya mato akanta. Kuma duk wani aikin daya danganci fita da ita ya datse sai dai in tare dashine kana yake barinta. Sosae wannan abu yama arms daɗi harda ma boss ɗin don kuwa dama da biyu ya turoshi naijan. Kamar dai yadda kuka san zaid baya taba aikinsa a gidan ko anan ɗin ma bata sanja zani ba don saiya ma zabi wuri mafi shegen taka yake gudunar da wasu manyan ayyukansa. Baki ɗayansu suna zazzaune ne a ƙayataccen babban ɗakin taronsu wanda suke gudanar da zama irin haka fuskan wasun su ko alamun rahama babu. Isa manu ne ya buɗe zaman jugurin ɗin da sukayi ta hanyar furta. "Billahil azeem ko kaffara ba zanyi ba dasa hannun wannan shegen yaron a kulle min ɗana" "Wa wai kana nufin _ÊÃGLÉ ÆK?_" Sukayi wata kakkausar murya ta faɗi wacce ya sanya suka shiga waige waigen ganin ta inda muryan ya fito hantar cikinsu na ɗurar ruwa. Kamar walƙiya haka suka kalla gimlawar abu shuuuuuuuu. A razane suka curo wuri gudu idanun kowannensu kamar ze faɗo ƙasa don tsoro, wata shefiyar dariya aka sake cekewa da ita tare da faɗin. "Hhhhhhhhhhhhh to kuwa tabbas kunyi kuskure don yanzune zaku fara girbar abinda kuka shuka Hhhhhhhhhhhhhhh" tayi dariyan tare leƙo da iya rabin kanta ta saman silif ɗin ɗakin Wata razananniyar ƙara suka saki haɗi da dunƙulewa wuri gudu duk cikinsu kuma babu me iya furta koda adda'a ce. "Duka a yanzu ne zasu fuskanci ainihin gaskiyar abinda kuka aikatawa mutum me daraja mutumin kwarai me zuciyar lu'u lu'u irin Naseer Baita Makole" A tare a sukane suka ɗago daga kawunansu duka ido kamar ze faɗo ƙasa, cikin wani kalan mugun firgici haɗi da tsoro da tsantsan tashin hankali yama ƙawanya suke duban saman silif ɗin saida battt babu ko alamar wata halitta. Kallon kallo aka shiga yi tsakaninsu ko wanne zufa na karyako masa, domin kuwa har gaban abada mutum ne da bazasu taba mantawa dashi ba a cikin wannan duniyar. "Yaki ya riga daya soma! ya kamata a nemi makamai domin yaƙar maciya amanar ƙasa, amma kafin ka soma kai ma kanka saika zamo makami. Bayan ka gano gaskiya to saika cika aikinta yazamo wajibi agareni domin ɗaukar fansar mumunin ruhin da kuka zalunta daga karshe kuma kuka sheƙe don haka yanzu loƙacine na girbar tarin abubuwan da kuka shuka" Baki ɗaya wutar ɗakin ne ya ɗauke A take wani mugun duhu ya mamaye ɗakin dulum ko tafin hannunka baka isa gani ba. Ihu suka shiga yi suna faɗin ta yafesu sun dena ta musu afwa ta musu rai. "Ba ko wanne kuskure akema afuwaba kamar yadda ba ladama ce tasa kuke neman afuwa ba kuna nemane sabo da tsira daga mutuwarku, Kunyi babakere a ƙasa kun hana matasanmu aikin yi wanda tsabar zalincinku yake sanyawa mutumin kirki ya koma bata gari, mata kuma suna faɗawa harkar zinace zinace duk ata dalilinku shin koda iyaka wannan alhaƙin aka barku ba'a barku da tarin zunufai masu nauyi ba. kun bata mana ƙasa kun sanya ƙasarmu ta zamo koma baya a ko ina akan sauran ƙasashen duniya kun kawar da iyalan da babi adadinsu. Kun kawar da shugaba na kwarai wanda tarihinsa bazai taba shuɗewa haka kuma bazai taba maimaituwa kun kawo wanda bama ɗan kasar ba kun bashi shugabancin ƙasarku! Wanda sammm babu koda ɗigon imanine a zuciyarsa wanda ƙasar sa mahaifarsa sukayi tirrr dashi ya gudu ƙasarku mara ƴancin kai me boye shegu a cikinta har kuka bashi mulkin da yake jagorantar al'ummarku ku burinku kawai kuga jama'a cikin mawuyacin hali. Inda kuke dariya a yayinda da kukaga mutunmin kirki ya koma mutumin banza bata gari cikin al'umma kuna ɗaukar manyan matsayi ku naɗa manyan malaman mu na addini a yayin da kukaga ya taso da ƙarfinsa, idan kuka bashi wannan matsayin shike nan kun gama dashi bashi da kata bisss ɗin daya isa aikata wani abu a kanku duk meye haka shin me mukai muku ne?..... Kusani awannan zamanin hatta tsuntsaye Allah wadai suƙe da wannan zamanin don kuwa laifinku na shafarsu ta hanyar ƙafewar koramai da Allah keyi su suka suna faɗuwa suna mutu da ƙonewar bushiyu gadai abubuwan nan birjik wanda duk nayuinsu ya ta'allaka ne akanku, wasu wuraren kuwa mutuwa mutane suke akan yunwa saboda da tsananin rayuwar da kukayi sanadiyyar jefasu. A yinin yau wani bawan Allah yaje har gaban shagon wani akan da ya temaka may kodade da sarakar garine amma haka wannan me shagon ya masa korar kare gefen shagon ya nema ha zauna tare da kife kansa akan ƙafafunsa!!!..... Kunsan meye faru? mutumin na zama Allah ya amshi ransa sai bayan mutane sun taru kana wannan me shagon ya dinga birgima yana kuka yana cewa wllh sai allah ya tambayesa don yasan mutuwarsa ta rataye a kansa. Kuma kumsan duk su waye sanadin hakan kune! Kune!! kun maida mutane masu Taurin zuciya da zafin rai kowa najin haushin ɗan uwansa duk su waye sanadi ku bani amsa ku bani amsa ku bani amsan tambayana mana su wa ye sanadi????......" "Mune wllh mune mune zamu gyara zamu gyara!!!" Suke faɗi a gala6aice cikin shiga ruɗu da mugun yanayi. "Amma dake Allahu ahaad yake sai ya bayyana muku ikonsa ta hanyar kawo wanda ma ba ɗan ƙasar ba yake seta muku hanyar ƙasar taku. Ba don haka ba da tuni ni nagama da babinku na shafe har labarinku a ƙasar saidai bana ma allah shishshigi a cikin lamurana duk da kasancewana ba mutum bace kuma ba musulma ba don haka zanbar mutumin kwarai yaci gaba da aikinsa na barku dashi shine daidai daku daidai da ƙugun ko wannenku domin shi mutum ne da aka haifesa don ƙawar da zulumci da maƙiya musulincin ku. Ni yanzu zan tafi my be ku ƙara gani na my be not my be for ever" Babat ta fa ce bayan ta gama gwara musu Jiki da haɗa musu jini da majina. Zaman da basu yi ba kenan ko wannensu ƙafa me naci ban baki ba suka ranta ana kare ko wanne sai maboyarsa. Wannan kenan. ☆✭ ★*** **☆✭ ★ ★★★*** Tsaye suke duka hankalinsu a tashe yake gashi ƙiran duniya oum tama Ak amsma wayan switch off. Sake kallan Meerah oum tayi bayan cike da tsananin tausaya a loƙacin da take sanar da ita cewa ta kwantar da hankalinta wannan ɗin ba wata matsala bace me girma don duk watan duniya tana fama da wannan ciwon. Har shashen oum babbar likitar dake kula da Emaar's tazo ta dubani tare da bani magun guna harda sadakar Injectoin na samu wanda dama kai tsaye nasan bazan shallake shanta ba tunda duk wani watan duniya saina amsheta. A wurin ne naji tana waya ita da mah wacce nake jin komai ta cikin wayar da yanda aka sha fama da Annena kafin ta amince ta yafe musu bayan bata labarin da sukay na yanda aka nemeta aka rasa har zuwa yanzun kuwa. A raina nake jinjina hali irin na anne na don dama nasan za'a rina wai karuwa tayi bari. Wuni guda kawai har na faɗa kasancewar dama haka jinyana yake loƙaci guda jikina ke komawa na majinyantan gaske. Da taimakon jesra na gyara jikina ina fitowa oum na shigowa hannunta riƙe da mug sai turiri yake dafaffen shayine irin nasu na labara wanda yake fidda wani irin daddan ƙamshi me rai da lafiya. Daga gefen bed ta zauna tana cewa na tashi nasha kana na kora da magani, Da ƙyar da lallamawa ta samu nasha saida da tabbar nasha kana ta fita. Data na kunna na shiga whatsaap bayan saimin sim card na ƙasar da jesra tare da phone wanda duka umarnin oum ne. Seta abubuwana nayi bayan nayi copy'n duka number's nawa na gida nigeria. Kamar wacce dama nake akan ƙaya abu na farko dana fara dubawa bayan gama seta komai na shine fara duba Sabon littafin _AMMEY LAYLERH_ Wato wannan ƴar baiwar marubuciyar tawa *MARYAM NASEER MIRRAH* wacce duniyar rubutu sukafi saninta da. _AMMEY LAYLERH_ ♡SPECIAL✯ _Ta Daban_ Wani mugun ihuuu na saki wanda ya sanya jesrah fitowa daga bathroom babu shiri, "Lafiya Uktiey?" ta ƙarasa fitowa jikinta duk kumfa tana tambayana. Banyi duba da kumfar dake jikinta ba na maƙalƙaleta ina sakin dariya kamar ba wacce take jinya cikin wani mugun farin ciki na tsantsan murnan da ya shige ni na shiga faɗin. _AMMEY LAYLERH! AMMEY LAYLERH!! AMMEY LAYLERH Ceeeeeeee" Kanta ta ɗan shiga jijjiyawa tare da kallon meerah ɗin tana faɗin. "Waye kuma Ammey Laylerh?" Dariya na sake saki tare da faɗin "Ki tayani farin ciki ta fara sakin wannan sabon littafin nata ♡SPECIAL✯ _Ta Daban_. ita dai jesrah kallon ikon Allah ta tsayayi sakinta tayi tana niyar komawa na sake riƙo hannunta ina faɗin tsaya ki gani. A take ta shiga cikin profile tare da group nata na facebook nan take ta fara nuna mata abubuwa. duk da ba ganewa sosai jesrah keyi ba amma ta ɗan fahimci abinda meerah ɗin take nuna mata. Tambayarta tayi sunan da take using dashi a facebook nan take ta faɗin mata. Bathroom ɗin ta wuce tana ce mata bara ta fito a bathroom ɗin itama sai tayi seach nata. Kamar da wasa kuma ta shiga telegram kamar wanda akace mata tayi seach na AMMEY LAYLERH tanyi saiga AMMEY LAYLERH ta bayyana dp nata ɗauke da hoton Wannan tsuntsuwar wato *MIKIYA* Sallama ta mata tare da bayyana mata cewar ita ɗin babbar masoyiyartace don Allah ta taimaka ta kulata, duk da kuwa cewar ta ganta a online amma sam bata sa ran zata amsataba. Amma kuma cikin abinda bai wuce 5min ba saiga reply ta amsa cikin mutumci. Wani kalan waro ido meerah tayi tare da riƙe baki ganin abinda ta rubuta mata itama tsabar ta shiga ruɗani sai kawai ta tura mata emoji na 😮 alamar buɗe baki da zare ido. A take ita kuma ta tura alamar na sakin dariya tare da rubuta yadai ƴan mata? _kawai nayi mamaki ne wllh_ _Na me fa?_ Ammey laylerh ɗin ta tura mata. _Yadda akai kika kulani haka ba tare da wulaƙanci ba_ Alamar zaro ido itama ta tura mata tare da mata rubuta sosae. _pls zan iya samun Number whatsaap naki pls don Allah!_ ta tura mata tare da emoj na abin tausayin nan. Number'n ta bata haba wa nan fa meerah ta sake sakin wani tsallen na tsabar farin ciki sai kawai tayi copy na no in takai cikin phone nata tare dayin sev da *Ƙauna* Whatsaap nata ta koma Sunan ƙauna ta nemo tare da mata sallam da gabatar da kanta itace meerah wannan masoyiyar tata. Dp na whatssap nata ta duba sai hotonta dake kai yayi saurin sauƙa na wata beauty girl ya bayyana tana tsaye Jin gine daga jikin bayan ƙofar parlour, screenshot ta mata ta tura mata tare da tambayarta wannan gurl in wacece? _MY LAYLERH_ ta bata amsa _Masha Allah ubangiji ya raya mana ita cikin aminci da yardarsa Aunt_ _Nagode_ Ta rubuta itama taga nan suka fira fitowar jesrah ne ya katse musu firan nan ta shiga bata labarin maganar da sukayi yanzu. Daga nan suka fita don merrah tace su fita su ɗan zaga ta gaji da zaman nan haka nan. gidan suka shiga zagawa tare da shishshiga ko ina har bangaren moh suka je. daga nan sukayi bangaren Ak suna daf da shiga oum ta ƙira jesrah a waya tace taje yanzu, cewa meerah tay tana zuwa amma ta ƙarasa ta sameta a ciki. Nan na kutsa kaina cikin ainihin side ɗin zuciyana na buguwa da sauri² ina jin gabana na faɗuwa sosae Nan fa ƙokofi suka rarrabe min nama rasa inda zanbi amma haka na shiga kutsa kaina cikin ƙofofin nan. Nanfa kaina ya juye nama rasa ta inda na shiga sai kawai na nemi hanyar komawa, amma itama ta bacemin batttt. Jikinane ya shiga rawa na shiga tafiya a tsorace ko ganin gabana bana yi chakkk na tsaya sakamakon tuntu6en da naji nayi da wani abu da bansan ko miye ba.......... To ai shike nan a gimtse👌 *By Ammey Laylerh* *🦅 MIKIYA 🦅* _A wonderful world & Special anti terroRism squad_ ____________________ *MARYAM NASEER MIRRAH* ~AMMEY LAYLERH ✍️~ ✯ *~🌠 JAJIRTATTU WRITER'S ASS.... 💫~* BOOK Two…………………………񆬍✍ 17&18 _DEDICATED TO ALL WRITERS ALL OVER THE WORLD_ ♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡ **☆✭ ★ Hot Reletionship scene **☆✭ ★ Hot love **☆✭ ★ Romance scene **☆✭ ★ ❤️❤️❤️ Wani kalan runtse idanuna nayi ina jin natsuwata na barin gangar jikina haka zuciyata ma na wani irin harbawa tamkar zata fice daga cikin kirjina. Jin na shiga tangal tangal ɗin faduwa ban ƙarasa dawowa daga duniyar ruɗanin dana faɗama naji an wani irin shatalan ƙafafuna ai kuwa na tafi ƙasa wanwas. Difffff dudif ji da gani na suka ɗan kauce na wani ɗan loƙaci. A hankali na shiga ware idanuna da suke cike da tsoro, A sannu gani na ya fara washewa tasss na sauƙe gani na a kanshi yana zaune fararen sawayen nan a miƙe, Gefensa kuma pipe ne na shisha da yake zuƙar abarsa hankali kwance. Wani yunƙuri nayi don bansan sanda wani shegen ƙarfi ya zomin ba "A uzibillahi minash shaiɗanir rajim!" na faɗa loƙaci guda kuma ina miƙewa tsaye sai dai bankai ga miƙewar ba na gan shi tsaye a gabana hannunsa riƙe da pot na shishan yana zuƙa da fesarwa, Hannuna na sanya da niyar rufe hancina ya sa nasa hannun ya fincikoni tare da sanya ni a tsaƙiyarsa ya tokare jikin bango yana fesa min hayaƙin bakinsa akan fuskana tare da tsareni da rinannun idanunsa da suka sanja colour. Bakina na rawa zuciyana na bugawa na girgiza kai tare da rumtse ido da ƙarfi a tsawace na furta "Mene haka wai?" Shiru yayi har loƙacin kuma be dena fesa min iskan shishan ba. "Wanne kalan rashin mutumcin ne wai kake haka? Malam ka janye jikinka a nawa ya dena taɓa fatar jikin Meerah don ba zan taɓa yafewa kai na ba idan hakan yaci gaba da faruwa, da babbar murya ina me faɗa maka ni Maryam Abdullahi Gwani har gaban abada jikina yafi ƙarfin wulaƙantaccen jikin..... Tsitttt nayi sakamon hannuwansa daya sanya ya zagaye jikin ginin da nake tokare har numfashinsa na sauƙa gefen wuyana. hayaƙin daya zuƙa ya sakr fesa min a fuska tari naɗanyi ganin wulaƙantani kawai yake son yine ya sani nai yunƙurin tureshi a jikina amma ko gezau beyi ba baki na buɗe da niyar yi may bala'i gabaɗaya na haɗiye hayaƙin daya sake buso min. Ai kuwa da wani irin sauri na fisge jikina a nashi tare da tattaro duk wani salive na cikin bakina na tofa may a saman fuskanci. Cikin duban ƙasƙanci na dube shi cikin tafasar zuciya "Allah wadai da duk wani me hali irin naka! Ko dan babu tantama ai dama dan ka zama ɗan shaye² ɗan daba irinka dama ai babu abinda bazai iya aikatawa ba ciki kuwa harda aikata sabon Allah". Hannu yasa ya hargitsa tulin gashin kansa kana ya furzar da iska me zafi daga bakinsa wani irin tsuma jikinsa keyi yayinda jijiyoyin kansa suka tashi ruɗu-ruɗu dasu tabbas tunda yake babu wani mahalukin daya taɓa yaɓa mishi magana kotankwacin wannan. {ABDOUL-MALEEK!!!} ya ji kamar zuciyarsa ta ƙiran sunan sane. kiran da sai daya ja numfashi ya haɗiye abinsa zuwa ciki ba tare daya fesar ba, yana jin hucin zuciyarsa na keto rufin fata bakwai da Ubangiji ya halitta a jikinsa. ja yayi ya tsaya a gabanta tare da ƙura mata idanunsa da suke lumshewa, har yanzu jikinsa ɓari yake numfashi yake sauƙewa a gwame kalmomin data jefashi dasu na neman suyi crosing mind nashi gaba ɗaya. A take idanunsa suka ita jirkicewa wani mugun bacin rai na dirar masa loƙaci ɗaya. Taku ɗaya tayi a na biyun taci ya damƙi ƙugunta tare da cirata sama ƙafafunta na wutsil² ɗin kwacewa. "Yau zan nuna miki hasalin yadda ɗan daba yake irin nasa aikinsa na dabancin, ki sani ko wacce ƙaddara tana da nata mafarin ke yau naki mafarin zai fara!. wannan shine mafarin taki ƙaddarar na kuskuren da kika tafka na shigo min har cikin bedroom na ba tare da neman iso ko izinina ba. Kana ki rubuta ki ajje to make you clear, tunda kikayi kuskuren shiga cikin kebantacciyar rayuwana don haka ba ki da wasu yara sai na wannan crimals ɗin, ba ki da wani miji sai wannan ɗan dabar, Kana ba wanda za ki yi wa takaba sai wannan dai shi ɗan dabar Ƴar Jarida Maryam Abdullahi gwani ta Abdoul-Maleek Hassan Al-hassan Emaar's ce har gaban abadan abadaaaaa!!!" Cilli yayi da ita kanta ya bugu da jikin rug ɗin ɗakin ta saki wata wahalalliyar ƙara riƙe da hannunta data bige sosae a hannun. Tsaye ta miƙe hannuntan na mata wani mugun zugi "Allah ya tsari gatari da sarar shuka! Har abada nafi ƙarfin mashayi ɗan daba irinka mugu! Azzalumi" Tana faɗar hakan ta kwasa a mugun guje ja da baya baya ya shiga yi yana komawa ya jingina da jikin caution ɗi dake ta bayansa. Wani shegen feshin iska be zafi ya fesar yana kaima iska naushi "Ouch!!!" ya furta yana sake kaima center table glass ɗin wurin naushi A take table ɗin ya fashe hannunsa kuma ya nutse a jikin gilasan ya fara zubda jini sosae. "Ohh shittt. Dom itt" Ya ɗaga hannun zai sake kaima table ɗin wani naushin yaji an riƙe hannun. "Subhanallah! Gargalion mi ka aita haka? Me kake shirin aikata be a man mana habeebty" juyowa yayi da sauri jin muryan oum saurin wurin da pot na shishan shi yake yayi ƙafansa yasa yayi saurin tura shi ƙarƙashin table ɗin. Hannun ta sake kamawa tana nufar ƙofar fita dashi hannunsa na tsiyayar da jini. Har bedroom nata ta shige dashi da kanya tayi dresing na hannun kana ta dubeshi cikin mugun ɗaure fuska. "Mene na gani a ɗakinka wanda ka tura da ƙafarka?" Saurin ɗago kansa yayi ya kalleta wani mugun kallo ta wurga may tare da faɗin. "Mene kake son maida kanka haka? shayeshaye har cikin gida ko kunyar mahaifinka dake cikin halin ciwo bakaji. Me kakeson komawa Abdoulmaleek?" "Oum!!" Ya faɗi yana ƙoƙarin kamo hannunta buge hannun tayi sai kuma ta juyo idanunta cike taff da kwallar da suka tara. "KO wacce ƙaddarar rayuwa tana zowa ɗan Adam ne ba tare da yashirya mataba, dalilin bashike da ikon Juya tarin ƙaddarorinsa ni kuma wannan itace tawa ƙaddarar. Ƴaƴana sune ƙaddara ya Allah ga bayin kanan ka shirya min su!!!. Ka tseratar min da imaninsu daga dukkan wani abu batacce ka tsare min su daga sharrin masu sharri ka musu katanga daga dukkan laifukan da suke aikata maka! Ya Allah kar kaci gaba da ba makiya damar cutatarmin da yara na YA RAHMAN........ Tayi maganar tane me rushewa da kuka. Wani irin tafasa jinin jikinsa ya soma tare da tsuma yana jin zuciyarsa na dunƙulewa wuri guda, Ja da baya da baya ya soma yana fesar da wani kalan zazzanfan numfashi. ko zogin hannunsa dake naɗe da bandagee baigi haka yasa kai ya fice zuciyarsa na tururi. Kai tsaye special room ɗin da pa'panshi yake ya nufa wanda yake a sassan nashi, zama yayi tare da tonƙoshe ƙafafunsa agaban mahaifinsan ido ya zuba masa yana jin abubuwa da yawa nason suyi losing nashi out. "Papa komai ya kusan zuwa ƙarshe a yadda kake ɗin nan babu ruwanka dama duniyar bare abinda yake cikinta da wasu ko kullum burinsu shine wawason abinda ke cikin duniyar. Ba mamaki zomo ya haifi kurciya, kurciyar kuma seta iya kasancewa unguluce wannan zoman kuma ba mamaki a wayi gari aji yayi gurnani kamar zaki!!!pa da kanka nake son ka tashi ka tunasar dasu cewar loƙacinsu ya riga da ya soma daga yanzun" Ɗan numfasawa yayi tare da sake riƙe hannun pah sai kuma yaci gaba da faɗin. "Duk da an shiga tsakaninmu dakai amma hakan be faru ba kamar yadda sukay zata! Drunker's kuma kaɗɗara tace bawai sawarsu ba kamar yadda sukai zata Zaid be lalaceba pahhhhhhh..... Kamar yadda duniya da ƙasarsa ke kallonsa duk a cikin salon aikinmune hakan domin yaƙar shege dolo ya kasance kaima shegen kan kane. Pahhhh!!! Zaid be taba koda kwatankwacin shan wani abu na maye ba domin nabi duk wata hanya na toshe hakan duk kuwa da nasan cewar ba wai iyata ce ta sanya hakan ba. Nima wannan ɗin shine ƙaddara amma komai da yake faruwa da bawa yana da nasa sanadin. Sanadin nawa an cutar dani tun ina ɗan ƙarami tun shekaruna basu kai ake bani wine as matsayin Coffee tun ba gane hakan ba harna gane daga ƙarshe naci gaba da siya da kuɗi. Amma hakan be taba gusar min da hankali koya fitar dani a hayyacina ba domin jinin dake gudana a duk wani sassa na jikina me ƙarfine kuma a tafashensa yake, A kullum kwanan duniya inama wine kallon lemu ne shisha kuma kallon flovour nima ɗan shaye shaye bane kamar yadda oum ta faɗi paaahhhhh kace mata "ABDOUL-MALEEK HASSAN AL-HASSAN EMAAR's KUWAIT ba ɗan smoker's bane ka faɗa mata papahhhhhh....... Kwallace ta zubo daga cikim kwarmim idon paaah hannuwansa suka fara motsawa a hankali sannu ahankali hannunsa ke motsawa harya ɗaga zuwa saman kan AK. "Na sani!!!" Paaah ya faɗi cikin muryan dayay low sosae da sosae wanda shima Ak ɗin iya motsin da lips na pahh ɗin yayi ya fahimta abinda yace ɗin, saurin jimƙe hannun yayi a ƙirjinsa hawayen da rabon da yayi harya manta na gangaro masa. A hankali paahh ya soma magana. "A loƙacin da duhun ke mamaye dani wani haske yazo ya haska min hanya! Daga nan shi wannan hasken ya disashe yabarni har gaban abada tun daga loƙacin na fahimta komai babu laifi hakan dan _SANYI YA HAIFA WUTA_ koba komai shine zai shige cikin wannan ɗayar wutar ya yaƙeta harma ya cita da yaƙi bayan ka gama kuma shi wannan sanyin yazo yamaka rumfa ya harma ya baka GARKUWA ko a yau a Yanzu raina yabar gangar jikina ba zan mutu dajin cewar na gaza ba zan mutune da kwarin gwiwar cewar na mutu nabar baya jaruma ba lusara kamar n............ "Nohhhhhhhhh paahhh har gaban abada kada kabar wannan kalmar ya fita a bakinka. Komai kuma Insha Allah za'a gama dakai kamar yadda aka fara tare dakai.don kaine hasken tafiyar kuma kaine jaruminta mu ubarni kawai muke cikawa muɗin kamar inuwarkane inuwa kuwa har abada bata taba magana bin umarni kawai ta sani" Jiki a matuƙar sanyaye ta ƙarasa shigowa don tun fitar shi zuciyarta ya gaza samun natsuwar tafiyarshin, tabbas duka maganganun Ak sun shigeta sun kuma ratsa jinin jikinta shin me yasa take mantawa da cewar komai na duniya idan ya faru da bawa akwai sanadinsa, Wani a sani wani kuma a rashin sani ne. "Sorry sorry double sorry Habeebty!!!" Oum ta faɗine tana rungume kan Ak ɗin. Numfashi ya sauƙe yana me sake ƙanƙameta "Oum baki min komai ba nine na miki laifi ki yafe min oum adda'ah itace gaba da komai kici gaba damin adda'a Insha Allah watarana komai zai zamo kamar ba'a taba yinsa ba" Kanta take jinjina masa don a yadda take ji bata da bakin magana kwata² Hannunsa cikin na pahh kansa a rungema a jikin oummey'nshi a haka wani daɗɗan bacin daya jima beyi irin saba yayi awon gaba dashi a wurin. Da kallon tsananin tausayi oum kebin Ak dashi tanjin soyayyarsa shida sauran ƴan uwansa naci gaba da huda ko ina na jikinta suna sake sake shigewa hasalin can can ƙasan ƙasan rai da ruhinta. _NIGERIA_ Victoria Island Wani shegen murmushi ya saki loƙacin da aka fara hasko labaran neman AK da ƙasa keyi ruwa a jallo. Zaune yake yayi crosing ƙafar nan ɗaya kan ɗaya yana sanye cikin wata brawn shirt da dogon wando kansa ba hula arms ne a gefensa yana sipping juice ɗin dake hannunsa na pine Apple. "Shirgi maganin bari ɗan oummey" Zaid ya faɗi yana shafan sumar kansa wanda hakan kaitsye al'a lanshine hakan. "Mazajen gaske ake magana masu sanya ƴan maza suyi hamma. Hadari sa gabanka inda kakeso" Arms yayi maganan da murmushi saman fuskan shi kwance dan ba ƙarya sunyi missing her Boss in nasu. Riyyace ta fito cikin shigar abaya maroon color tayi rolling da vail na abayar sosae tayi wani kalan kyau na fita garari. "Ina zakije?" Dakakkiyar muryan zaid me kama data Ak ya daki kunnuwanta. "Zan fita shan Ice cream ne bro" Be ko kalli inda take ba ya furta "Ko ma babu inda zakije!" Ware ido tayi tare da kwalalosu gaba tana ja baya. "Ha ba yaya pls wllh na kwana biyu ban fita ko ina ba tunda ka dawo" "Say I Sey get out in my room nace miki koo?" Bakinta ta ɗan tura gaba tare da komawa bedroom tana dab da barin palon taji wannan hosky voice nashi na faɗin. "Change our mekeup kizo mu fita" "Raelly Yaah?" Ta faɗi cikin zumuɗi "Na taba miki ƙaryane?" Shima ya tambayeta yana mikewa don sanja shigarsa shima. Kusan loƙaci ɗaya suka fito shi sanye cikin wani tsadadden yadi me laushi ita kuma babu komi a fuskanta kuma ta sanja shiganta da atampa duguwan riga Esherp sai brown jalbab ɗin data saka. A tare suka sakarma da junansu murmushi har suna rigerige wajen faɗawa kowa ɗan uwansa yayi kyau. A wata lafiyayyar jeep suka fita blue black sai mota ɗaya tak da ta rufa musu baya shima kuma hakan bisa umarnin arms ne, don gudun samun sabani duk da kuwa baya fatan hakan. ★★**★★★* Isah manu na zaune a parlour'n cikin wani gidansa da yake ganawa da ƴan siyasarsu wanda yake rufama baya su taka duk matsayin da suke son kaiwa a kujerar Mulkinsu. duban CSP chief Superintendent of Police yayi tare da faɗin. "Gaskiya nayi mamaki daka gaza ko wanne katabus akan wannan cese na Daddy's boy, karka manta da cewar wannan matsayin mune muka baka amma ace kana ƙasar nan kana cikin garin nan ɗana yana a hannunku amma ka gaza yin komai akan hakan! Kana ga Farouq dama bamu san a wacce duniyar shi yake bama amma duk kayi shiru duk maye haka kodai ka fara gajiya da aikin ne?". Isa manu ya faɗi a tsawace yana me dakar table ɗin gabansu dake shaƙe da tarin juice. "Karka damu Boss wllh ina kan shiga da fice akan hakan nima kuna ta ko ina na baza yaran mu kuskure Kaɗan kaɗan na iya tarwatsa komai akan dik wani shiri na AK!. Wanda kai tsaye tsananta binciken da nayi akansa yasa na gano wasu muhimman abubuwa game dashi saidai akwai girgiza zuciya labarinsa" Wani hucin zafi Hon isa manu ya fesar. "Kaje maganarka kai tsaye kwalba" ya faɗa yana sauƙe numfashi. "Shi ɗin ba cikakken ɗan ƙasar Nigeria bane wani muhimmin aikine ya jehohi nigeria daga ƙasar KUWAIT!" Dukansu a razane suka miƙe suna kallon kwalba ko wannensu bakinsa na rawa amma kuma ya gaza furta komai. "Kuwait ɗin da yake amfani dashi bawai ado bane da ƙasar shi yake amfani, shi ɗin SS ne kuma soldier yazo kuma nigerian ne ta hanyar yaudara da cin amanar ƙasa. Abu mafi girgizawar kuma shine shiɗin Ɗan Masarautar EMAAR's ne ɗaga sarki Hassan Al-Hassan EMAAR's Kuwait Jika ga marigayi ASHAAN ZEEN Bin Dawood! Yazo ya mana basaja a cikin kasarmu harya shiga ƙungiyar soldier na Nig ba tare da ansan koshi waye ba duba da cewar bama dubi da nikname na mutum manyan mu sun sha adone irin na suna don ya ƙawata sunan yake amfanin da kuwait. Amma komai yazo mana da sauƙi don yanzu haka akwai tarin pisc nashi da nake dasu da yawa kuma shiɗin twins ne kamarsa daya da biyuninsa wanda na samu tabbacine daga cikin masarautar nasu!" Tsawa yayi tare dabin kowannensu ido don duka jikinsu a daskare yake da dukkan alamu jininsu ya tsaya da aikine zuciyarsu kuma ta tafi hutun rabin loƙaci lol😀😊😅😃😄. Ci gaba yayi da faɗin "Sai dai a cikin masarautar tasu ma kanta ba'a gyare take ba ba'a tsabtace take ba domin kuwa gurbatattun cikinta sunyi masu tsarkinta yawa. Kuma da shine aka ɗaurama Matashiyar ƴar jaridar nan _MARYAM ABDULLAHI GWANI_ Aure bisa wakilcin kakansa Sarki _SURAJ SHUREIM_ (Sarkin kano) Wanda a zahirin gaskiya sune suka tarwatsa aurenta da yaronka salman wanda Akai aiki da rashin kaifin tunani irin na mata Akayi amfani da Yayar matarka wajen haɗa aurenshi da yarinyarta surry. Wanda dama ido rufe take neman duk wata hanya da zata ga ta samu wajen ruguza auren sai kuma gashi ta samu hanya mafi sauƙi wannan shine dalilin. A yanzu haka komai nasu yazo hannuna sir. Loƙaci kaɗan kawai naje jira *BOOM* komai ya fashe ya tarwatse don idan har banyi nasara a cikin wannan aikin ba niɗin bani baneeees" Da wani kalan mugu mugun mamaki tsoro ruɗu rawan jikin duka suke kallon kwalba dake dariya irin da ƴan dabar nan. Hannunsa na rawa yake nuna kwalba as (CSP chief Superintendent of Police} "Kana nufin duk wanan aikin wannan shegen yaron ba hasalin ɗan ƙasar nan bane? Bakin haure shine zai shigo har cikin ƙasarmu ya sanya mu gudun tseren tsira yake gwara kawunanmu kaiiiii wllh Inposible never never never wannan ɗin bama mai yiyuwa bane har gaban abada" "Idan da ba mai yiyuwar bane da duk hakan bata faru damu ma manu tabbas wannan gaskiyane" Kwalba ya faɗi yana zube tarin pisc ɗin Ak dama na ahalainsa baki ɗaya ciki kuwa harda Merrah. "A..K..A duk ata sanadinsa komai daya farun damu ya faru, don haka yana da buƙatar tsaro na musamman don kaucema afkuwar wata sabuwar matsalar. Merci à tout ceux qui essayent de gâter nos noms auprès des autres. Continuez seulement Dieu connaît bien les gens" Har rige rigen ganin pisc na Ak suke duka kusan a tare suka ɗago a razane. "Wannan ai Empire labeeb ne yaron dana fi kowa yarda dashi a cikin duniyar nan" Cewar Audu bashasha "Empire labeeb ko kuma Chakes yaron dake mana aiki a duk wata sabgar shiga da ficenmu ta fasa ƙauri" "Hiiiiii nifa gaba daya kaina ya gama kullewa taya za'a ce bullet duka shine me dame nene naku ni ai ko a jiya na zauna dashi tare da wannan yarinyar yar" Zubairu tanbuwal ya faɗi yana zaro wayarsa ya nuna musu pisc na Zaid tare da REEYYA wani kalan zaro ido audu bashasha yayi. "REEYYA againt kenan wannan yarinyar AK ke?" ya faɗi yana juya musu wayar haba nan da nan kowa ya shiga kallar kowa kenan kowannensu yana aikata wani mugun abin ba tare da ɗan uwansa ya sani ba. Kallon kallo ake me cike da tuhuma da kuma ƙarin bayani jikin ko wanne na ketowa da zufa. Ganin kowa dai nada nashi tabon yasa kowannensu danne ƙawa zucinsa akan ɗan uwansa cikin ƙanƙanin loƙaci suka baza pisc na zaid As (AK) Kan duk inda aka gansu ayi ram dasu idan kuma sunƙi kamuwa a basu wuta.... ****** Fitowarsu Kenan daga cafee cikin nishaɗi bayan sun gama shan Ice cream da sauran kayan maƙulashensu suka biya ta cafee ɗin don cirar wasu takardu da Ak ya turo musu. Suka ji an buɗe musu wuta a bazata abin yazo musu don sammm basu tsammaci hakan ba, "REEYYA go the car" Ya faɗi da ƙarfi a kuma daidai loƙacin arms ya cilloma zaid ɗin gun tare da faɗin. "ZAID Amshi nan" wani irin juyi yayi cikin salo gwanin birgewa yayi katan tanwa a sama tare da cafkar bindigar yana dire ƙasa tare da soma meda musu da martani. Kuma duk wanda ya seta seya harba cikin wani irin birgewa da salo na daban don salome me tafiya da duk wani me kallonsa. Ta bayansa wani ya tare da seta harbi a damtsen hannunsa kafin ya kai ga harbawar yaji an harbi kafafunsa a take ya zube ƙasa kan gwiwowinsa. Wani irin tashi sama Zaid yayi tare da bi ta kan motocin yana sakarma wanda ke ƙoƙarin Reyya harbi bayan ita ta harbi wanda yazo da niyar harbin zaid ɗin. Cilak ya ɗauke ta yana dirar da ita ta ɗaya gefen nan itama ta fara bada wuta duk kuwa da yadda yake faɗin Ta kuma amma taƙiya, Fafatawa sosae akai tsakanin su zaid da da waɗan nan yaran ganin dai tabbas ba riba a yaƙin ne ya saya su guduwa. Tsalle ɗaya yayi ya faɗa saman motar yana crosing ƙafafunsa yare da duba takardun da Ak ya turo masa baya nai ne akan cewar lallai yayi taka tsantsan don wani daga cikin ƙasarsa ya buɗe masa aiki. Yanzu shiɗin bayyananne na ga mayunwatan zakunan ƙasar Nigeria. Wata kafurar dariya zaid ya saki loƙacin daya ganin komai "Wasa a bayyane ai yafi daɗi DUD! ta haka kafi saurin fahimtar maƙiyinka saikace ba taken salonka kenan ba Akiey I love the games" Ya faɗi duk kuwa cewar da harshen larabci yayi hakan be hama arms fahimtar abinda ya faɗi ɗin ba. Shima dariyar yayi don shima ruwan tafe ne me haɗi da cida yafi son komai za'ai ayishi a buɗe. Amma kuma yasan dalilin Ak ɗin na rashin bayyana kai da beyi ba badon tsoro bane sai dan tsaro. A yanzu kuma ya tabbata wasan yazo ƙarshe tunda komai ya gama buɗewa yanzu ainihin wasan ze fara...... ***** Kamar an cillo shi daga sama haka Reza ya faɗo cikin Palon Isa manu jikinsa na rawa. Tsaye ya miƙe shima yana duban rezan tare da faɗin "Fatan aikin dana baka haɗi da binkicen nan ne suka kammala right?" "Ka saka rayuta a haɗari shine kake tambayana kammaluwar aikinka? Sai kuma ya wani karkatar da bakinsa kana yaci gaba da cewa. "To Allah be ida nufinkaba na kasheni ka biya min kuɗin jirgi don kawai naje ga mutuwa tane ashe, to ka sani Company'n (E) GROUP bana kowa bane se ÊMÆÃR's WORLD INTERPRICESS COMPANY. Cikakken Companyn ÉAGLÊ ne AK ĒAGLÉ!!!. Kasan kuwa ma'anar ÉAGLË? Wata tsuntsuwace wacce idonta yake zagaye da komai dake wakana na cikin duniyar! Shi kuma to harma yafi hasalin me sunan aljananci domin kuwa shi ɗin ya kasance da ido ɗaya yake bacci ɗayan kuma yana gadin duniya domin kareta daga balagurbi irinku. Hasalin cikakken labarinshi aka zaunar dani aka bani Shima yace ɗaya ne daga cikin Ahlinsa sunan shi ma ASAAD EMAAR's kuma shine ƙashim bayansa. Shike gudanar masa daduk wani harka na business nashi. A takayyace wannan AK ɗin kobe haɗa da matsayinsa na SS, SOLDIER,DSS,PILOT, ba yana da ƙarfin ikon da zai iya batar da duk wani mahaluƙi da yaso a cikin wannan duniyar ba tare dako an sake jin labatinsa. Duka duniyar ya kewata ya kanainayeta da dukiyarsa da zuciyarsa shi ɗin me ƙarfin ikone a kowacce ƙasa kuwa. Shiɗin mutum ne me zuciyar lu'u lu'u amma in aka taba shi yafi boom cika aiki na barka lafiya kada ka sake nema na akan AK. Mutum daya gagari duniyar ma baki ɗaya bare ku to idan da za'a buɗe maka maka manyan ƙasashen duniya da aikinsa yabi ta kansu da saikayi rawar banjo ba tare da kiɗi don haka I DON'T CARE MANNER's don AK Idon duniya ne me bacci da ido ɗaya, haƙarƙari ɗaya don bema adalci gaskiya don kawar da bata garin cikin al'umma me ɗebe matasa irin mu wanda halin babu yasa kuke amfani damu wajen sanyamu yi muku aikin kisan rai me makon ku temaku amma kune kan gaba wajen lalacewar _ƘASAR NIGERIA_ Kunje kun boye ƴaƴanku a gidajenku koma ku haurar dasu ƙasashen waje mune ma manyan jahilan jakunan da muke biye ku akan wasu ƴan kuɗaɗe ƙalilan kuna me damu ƴan dabar ƙarfi da yaji ALLAH BAZAI TABA BARINKU HAKA BA! AK kuma shine maganin irinkuuuuuuuu" Har wani mayen hayaƙine ke fita ta kunnuwan isa manu loƙacin da Reza ke kwararo masa jawaban nan. Be gama dawowa daidai ba yaji shigowar ƙira ta cikin landline ɗin palon "BOSS aiki yaci ruwa ya taka laka bi ma'ana aiki ya kwabe mana wannan mutumin kuwa anya ba aljani bane" "Ɗan kunama me yake faruwa? sanar dani ka sanar dani yanzu" "EAGLE" Sunan daka bamu a wancan loƙacin yau munyi ido huɗu dana zahirin bawai sunan ba, don haka se wata rana nida ka ƙara jina har gaban abada" Ƙitt ƙitt ƙitt haka yaji ƙarar datse ƙiran duk yadda yaso da trying no Ɗan kunama abin yaci tu rah. Wata iriyar zufa yake sharcewa a jere a jere ƙiran mutanensu ya dinga shigo masa amma yana gani duk yayi Ignoring nasu. Don a yanzu likita kawai yake da buƙayar gani ba kowa ba don kuwa yana ji a jikinsa jininsa yahau fiye da sau cikin masaƙi. Da baya baya ya shiga ja harya dangana da rug ɗin palon zaune yakai zuciyarsa na neman yin bindiga ta faso ƙirginsa ta fito....... *BY AMMEY LAYLERH* {Mirrah} *🦅 MIKIYA 🦅* _A wonderful world & Special anti terroRism squad_ ____________________ *MARYAM NASEER MIRRAH* ~AMMEY LAYLERH ✍️~ ✯ *~🌠 JAJIRTATTU WRITER'S ASS.... 💫~* BOOK Two…………………………񆬍✍ 19&20 _I DEDICATED TO ALL _MY FAMILY's ƘOFAR GABAS da ƘOFAR FADA da NASARAWA_ Hhhhhhhhh karfa ku dumu Duka family's nawa ne Amma hasalin mahaifar nawa NASARAWA ne inda na RAYU tun daga yaye a ƘOFAR FADA kuma BABBAN MASALLACIN JUMA'A, A wurin kakannina. ƘOFAR GABAS kuma itace mahaifar ABBANA. UBANGIJI YAKAI HASKE ƘABARINKA ABBANA! MAHAIFIN DA BANA DA KAMARSA ADUK CIKIN DUNIYAR!......I MISS YOU MY ABBANA!........ ♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡ **☆✭ ★ HOT LOVE**☆✭ ★ **☆✭ ★ ROMANCE SCENE**☆✭ ★ **☆✭ ★ DEEPFRIENDSHIP**☆✭ ★ **☆✭ ★KUWAIT. Zaune yake kan wata luzury coolest rug me ɗauke da disigne na C ƙafafunsa zube cikin swimminpool ɗin, hannuwansa kuma ya naɗesu akan kujerar ya ɗora kansa akan hannayensa. Daga gefensa kuma Extreme milk shake ne da strow berry syrup se pink edible glitter. Ahankali yake sipping Vanulow Ice Cream ɗin idanunsa a lumshe sanyi da kuma garɗin Ice cream in na ratsa bakinsa da kan halshensa. A hankali take zagaya garden ɗin wanda yau kwananta uku kenan da fara zuwa. Wanda ta can bayan window's ɗin room nasu ta hangi garden ɗin me ɗauke da ni'imomi kala daban daban. Komai daya danganci ƴaƴan itatuwa na laraba babu abinda babu a cikin garden ɗin, Sanye take cikin riga da wando na palazzo vizom ride se band cap ɗin dake kanta pict color. Kanta a sama don babban burinta takai ga fasa dabiir ɗin da take hange tun daga nesa. Samm sammm bata kula da ruwan dake wurin ba bare aje ga wanda yake zaune a wurin. Ƙamshin wurin yaj ga baki ɗaya na sanja masa da wani unique ƙamshi na daban, A hankali yake ware lumsassun idonsa da bacci ya fara rinjayarsu kaɗan bada yawa ba. Zuciyanta ɗaya take sake tun karar wurin befi taku ɗaya ba ya rage tsakaninta da faɗawa cikin swimming ɗin. Be tashi a inda yaken ba haka kuma besan ta yadda ze ceceta daga faɗawa cikin ruwan ba shiba mutum bane mugu bare Ya kalli wani rai me numfashi na shirin cutuwa ya ƙyale. (Ze iya iyuwa yarinyar bata iya ruwa bafa) Zuciyarsa ta raya masa gashi ta cira ƙafar kenan daya mata tsawa kuma babu mafaka faɗawa cikin ruwan zatai haka kuma kafin yaje gareta nan ma ta faɗa cikin ruwan. Shi kansa ba zaice ga sanda bakinsa ya buɗe har ya furta sunan. *☆MIFRAH!♡* Wanda hakan yay daidai da faɗawanta ruwan tumjim. Cikin abinda bai wuce ƙiftar ido ba shima sai gashi ya faɗa cikin ruwan yana danna iyo a cikin ruwan domin sai yanzun ya tuno da _ORCAS FISH_ ɗin dake cikin ruwan wanda kai tsaye zasu iya cutar da ita. Cikin wani irin mugun salo ya sake yin ƙasa luuuuu a can ƙasan ruwan loƙacin daya hangeta yayi daidai da sanda wani ƙaton Orcas yayo kanta. Wani kalan zillo yayi tare da bugar kan fikin da ƙafarsa ai kuwa kifin yayo kansa gadan gadan. Cikin rashin tsoro da sabawa da wasan da yayi dasu dama can tun husil ya jefa may ƙafarsa kifin kamar wani mutum ya buɗe manyan idonsa like na mage akan AK. Ƙafar ya sake shura masa yana yin ƙasa daidai ta ƙarasa ƙarshen ruwan jikinta na sakewa baki ɗaya. Rungumota yayi a jikinsa ya fara tafiya da ita a cikin ruwan. Yanajin jikinta babu alamun numfashi akan wata chiepgago catasiam chiar ya shimfiɗeta tare da zuba mata idanunsa da ruwa suka shiga ciki. Yana gaza tunanin ma wanda taimako ya kamata ya fara bata kawar da kansa yayi tare da ɗora hannunsa saman ƙirjinta setin wuyarta ya fara dannawa 6ull saiga ruwa ta hanci ta baki yana bulbulowa ci gaba yayi da danna kirjinta nata idonsa ba'a kanta ba gashin kanta a tarwatse band tayi nata wuri tare da ribboms ya baje har saman ƙirjin nata. Fara fat haka fatar ta yayi a take saida ruwan ya gama fita tsaff amma kuma bata kawo numfashi ba alamar somewa tayi kenan ta tsorata da ya hala. Yi yay kamar ya ƙyaleta amma kuma wata zuciyarta na faɗa masa ko ba komai ai tana da haƙƙi akansa. Idanunsa yaja ya lumshe tare da ɗora bakinsa saman lips nata ya fara hura mata numfashinsa me ɗumi. Wani gwairon numfashi tayi tare da soma tari saurin ruwan na ƙarasa fitowa. A zabure ta ware dukan girman idanunta jikinta na kakkarwar tunowa da kifin da yayo kanta. Buɗe baki tayi da niyar Kwalla ƙirar sunan Anne'nta amma sai taji wani al'amari na daban ƙarasa sauke ganinta a kansa tayi lips nashi cikin nata idanunsa a lumshe eyelashesh nashi na ɗigar ruwa da gashin kansa shima, Ash ɗin rigar dake jikinsa armsless na ɗigar ruwan itama. Jin alamun ana kallonshi da motsin farkawar da tayi ne ya bashi damar buɗe idonsa da har yanzu ruwan kmda sukar shigar masa na ciki. kafe cikin nata idanunta yayi da nasa cat eyes ɗin masu matuƙar girma da yalwar gashin da haryanzu ke ɗigar ruwa, kif-kif kawai ta shiga yi da idanunta  gefe guda kuma sai faman kokawa take da numfashina dake seizing.          A matuƙar wahalce ta samu ta kwace lips nata daga bakinsa tana sakin doguwar ijiyar zuciya tare da buɗe bakinta da niyar masa tsiwa da karta masa rashin m akan kada ya sake shiga harkanta. Chakkk maganar da take niyar yi ɗin ya maƙale mata a loƙacin daya jefa idanunsa cikin nata, maƙut ta haɗiye maganar nata dan duk yanda ta ƙudiri niyar masa tsiwa da karta masa rashin m kasawa tayi.Don shi Mutum ne mai masifar kwar jini da cika wuri ALLAH ya azurtashi da wani irin baiwar da duk tsagerancinka baka isa yi may ba a loƙacin da yasa idonsa a cikin naka koda ace ya fisa a shekaru kuwa. Wani irin kwarjini gareshi na ban mamaki don tin muna nigeria saina kuɗiri niyar may rashin mutumci amma samm bana iyawa sai a bayan idonsa ko ya ɗauke ganinsa akallona. Ƙoƙarin janye idona nake a kansa amma ya hana hakan ta hanyar sarke nawa idon a cikin nashi. Wani kalan smile ya saki tare da janye jikinsa daga gareni.Yanda yay murmushin ne yasa har ban san yadda akai na kafesa da mayataccen kallo ba.  Idanunsa ya ɗan waro min waje da ɗagesu alamar kallon fa?. Cikin sauri na kauda fuskata gaba ɗaya ina murguda masa baki tare da faɗin "Miye abin kallon ma a wurin crim irinka?" ƙasa ƙasa yadda nasan bazai jiba. Amma ɗan bawar Allah'n nan tamkar kunnen maciji ashe saida yajini saijin sauƙar deep voice nashi nayi daf da fuskana yana me faɗin. "Kuma a haka dai kika gani har kika mato kika ce Inba ɗan ƙasar kuwait ba sai bakim rijiya" wani kalan zaro idanuwa gaba nai tare da furta. "Wllh ƙarya kakemin uhumm jannnn toma nayi me dakai?" "Abinda ake yi mana" Saurin kallonshi nai gabana na mugun bugawa tare da faɗin. "MII YE A AH KEYI ƊIN?" Na faɗi cikin rarrabewar murya saida ya kwashi wasu second kamar kuma daga sama naji sauƙar muryansa yana furta "Nima ban sani ba" (Ɗan ikka) Na raya a raina kallon yadda fitar numfashina da kuma sauƙarsa yayi saiji nayi baki ɗaya ya dawo jikina tare da feɗin. "Waye ɗan ikkan" "Innalillah ni yaushe ma kaga nayi magana?" Na faɗi cikin marairaice murya kamar wata ta gari. "Nan ne ya faɗi kuma na tabbata baya ƙarya" Ya faɗi yana me ɗora hannunsa akan dede setin maƙogwarona. "Wllh ni banason sherri kuma saina haɗaka da Oum!" fuskana yaɗan lakace tare da furta "Really? Kuma me zakice mata? ce mata zakiy mijinkine yay........ Ai ban ma san sanda na rufe masa baki da hannu naba ina wani zazzara ido irin an kama barowon nan yayima sarki sata. Kamar kuma an zabure na tattaro duka ƙarfin daya min saura na turashi gefe ina kwasa a guje ba tare dana bi kota kan sauran kayayyakina ba. Da wani kallon kallo yabi bayanta yana me sauƙe ijiyar zuciya. Ɗagowar da zaiyi yaga gittin mutum halamar kar a ankare da koma waye kenan. Zuciyarsa yaji tana tafasa namomin jikinsa na ɗaukar tsuma kenan duk yadda yake taka tsentsen da rayuwar da kuma sirrinsa se ankai ga wani ya gani kenan. Lallai anason kaishi bango ne kawai domin suna daf da ƙarasa balle ramin kurane da kansu. Wanda daga karshe kuma farautar da zaiyi bame kyau bace. Jikinsa na ɗigar ruwa yabar wurin yana bi ta ƙofar daya shigo ƙebantacciya. Kai tsaye jerin floor'n dake zagaye a Downstairs ya faɗa cikin ɗaya be ɗau wani loƙaci me tsayi ba ya fito babu riga a jikinsa sai wani farin trouser dake jikinsa guntu.       Upstairs nashi ya koma first floor inda nan ne bedroom nashi yake kai tsaye bathroom ya wuce yana me sakarma kansa shower, Jikinsa sanye da bathrobe ya fito se wani mini towel ɗin da yake amfani dashi wurin tsane gashin kansa. Cikin zafi zafin da zuciyarsa ke masa ya shirya kansa cikin wasu halp armanian caftan, second floor ya nufa sumar nan ta baje ta rufe duka kusan fuskan shi. Cikin master bedroom nashi ya faɗa inda nan ne ɗakin nu'urorinsa a nan yake gudanar da duk wasu ayyukansa. Kai da ganin ɗakin ka iya rantsewa dan ijiyar na'urori kawai aka yishi. Don ita kanta ƙofar babu wani mahaluƙin daya isa shigarta idan har ba me ita ba duk kuwa da yadda kakai da iya bin kwakwaf ɗinka.      Ɗakin ƙaton gaske ne na ban mamaki yana shiga ƙofar ta rubuta _Welcome to A...MALEEK linor_        Da silver and golden metals masu sheƙi wanda ke ɗauke da salon burgewa akan wata casion sofa ya zaune nan ya shiga jona na'urorin yana kunna kowacce. Na duka sassan garden ɗin don so yake yaga tun yaushe aka fara masa irin haka. Abin mamaki kuma footage camera ɗin bata nuna may komai ba se shigan Moh da kuma yadda ta fita kamar a tsorace daya gani. Sai kuma Shigan Meerah tun daga ranar farko har zuwa yau da yanda take zuba shirmenta. Be murmusaba be kuma ɗaure fuskan ba don shi ba mutum bane da ake iya fuskan yanayinsa kai tsaye. ***** Meerah ____ A nutse take cira ƙafafunta amma kuma daga can ƙasan zuciyanta tsoro ne fall na yadda al'amura suka faru cikin abinda basu wuce seconds ba. Tsabar kanta ya rikice taka mai mai seta rasa hanyar da zata komawa bangaren oum ɗin. Don gini ne masu yawa kuma kusan iri ɗaya wanda dole idan baka saba rayuwa a cikinsa ba kanka ya ringa rikicewa wajen banbantasu. Wani matsananci faɗuwar gaba ta tsinci kanta a ciki. A ranta tana rasa miye dalilin daya sa duk sanda zan haɗu da matar nake tsintar kaina da faɗuwar gaban. Saima na rasa ta yanda zan saisaita tunanina na gane ainihin abinda yake haifarmin da hakan. Maganganun da kunnuwana suka jiyomin daga gareta ne suka sanya ƙirjina wani irin dokawa wanda kai tsaye hakan ya dirar min da wani matsanancin ciwon kai tare da zazzabi me zafin gaske. A take jikina ya shiga rawan sanyi dama kuma gani da jiƙaƙƙun kaya wanda dama nasan babu tantama sai hakan ya haifarmin da zazzabi ko mura nayi ta atishawa ba kakkautawa shi yasa sam bama ga maciji da ruwa, Da baya na soma ja idanuna nason rufewa daga kallon gabana amma ƙarfin hali da taurin zuciya ya sanya naki bama hakan dama ta hanyar hanasu kullewar, ga wata shegiyar jirin dake ɗibana amma haka nake takawa inaja cikin ƙarfin hali. Daf da shiga ƙofar palon tayi baya luuuuu anan jirin ya sama galabar kayar da ita. da sauri Aafia ta fitowarta kenan daga sassan oum ta tarota tana ɗora hannunta saman hancinta taji koda sauran numfashi. Jin babu alamar numfashin ne ya sanyata Komawa passess na oum ɗin, babu daɗewa sai gata sun fito tare da oum da jesrah. Tub fitowar oun bayin dake jere a layi Suke duka mata wasu na zubewa idan sun ganta saboda girmamawa saidai Sam hankalin ta bekai garesu ba saboda da tashin hankalin da take ciki akan meerah. "Kama min ita Aafia mu kaita ciki" da "to" aafia ta amsa ta suna shigar da meerah can cikin bedroom na oum. Zama tayi a gefen lallausan gadon ta Wanda yaji ado da tarin mayafai irin na sarauta ta cire alkyabbar dake jikinta. Wayanta ta ɗauka hankali tashe kai tsaye gargalion tayi calling. "Gaga maza yanzu kazo duk abinda kake ka fatse shiiii Maerayamah ce babu lafiya!" (Maerayamah) ya maimaita sunan acan ƙasar ranshi yana tuna waye ma me irin wannan sunan a gidan, ba tare daya ko tuna me sunan ba ya datse ƙiran yana fitowa daga cikin computer room ɗin daya ɗebi loƙuta masu tsayi a cikinsa yana charking out na duka ma abubuwan da yake da buƙatar ganinsu. Cikin abinda gai gaza Five minutes ba sai gashi ya shigo har bedroom na oum ɗin. Akan wata chalkia sofa ya zaune me launin L yana me fuskantar gadon. "Da buƙatar ka fara rage mata kayan jikinta da dukkan alamu shine ya bata damuwan" yaji muryan oum na bashi umarnin hakan kai tsaye. Kallo ɗaya yama inda take kwance ya ɗauke kansa a kallonta. Tsammm ya miƙe tsaye be ko kalli inda oum take ba ya ɗaga ta cilak yana fita da ita baki ɗayanta tamkar wacce ya ɗauka jaririya. Lallai sai yau na sake tabbar da cewar mutumin nan ba ƙaramin ma'abocin gym bane duk ilahirin jikinsa a mummurɗe yake alamar ƙarfi sosae ta bayyyana a jikinsa. Cikin wani eltia room ya shige Kana buɗeta za ka tadda upstairs wadda ta yi sama, in ka bi ta za ta kai ka dakunan bacci ne guda biyu dake jere. Ploor ne me girma haka amma ba irin girman nan sosae ba, wanda ya qawatu da kujerun fata masu taushi da santsi, gefe guda kuma na’urar dumama daki (room heater) Akan doguwar caugh ya kwantar da ita. Jiƙaƙƙun kayan jijinta ya fara zare mata tare da ɗaura mata towel ɗin daya gani. A hankali yakai lips nashi saman lips nata, saurin zame bakinsa yayi jin yadda ilahir jikinta ya ɗauka wani kalan zafi sosae me turara jiki. Meyarwa yayi tare da fara zuƙo numfashinta ya jima kafin ya samu tadakyar taja wani gauron numfashi. Fatar idontane ya soma motsi alaman tana son buɗe idon ne amma kuma yaji² da raɗaɗin dake mata ne ya sanyata gaza buɗe idon. A hankali bakinta ya fara motsi wanda bakajin abinda take cewar, ido ya tsurama bakin nata take ya soma fahimtar maganganun da dake faɗi cikin can ƙarshen sauti. "Anne! Wannan gidan ba gidan zama bane domin kuwa sonkai da zalumcin dake danƙare a cikinsa ya zarce sanin me tunani! gidane da yake daf da tarwatse wanda ƙarfi da yaji ake son zalimci yazam shine gaba da komai na gidan. Oum! Anne don Allah karku bari hakan ya taba faruwa don Allah Oum me kika ma waɗan nan mutanen suke son ganin bayanki har ƙarshe? Oum....... Bakinta ya rufe da nasa bakin yanajin abinda ya tokare ƙirjinsa ɗazun yanxun na shirin dawo masa. Sai kuma a hankali ya zare bakin san tare da tsareta da dukka manyan idanunsa A kanta, "Mene yaba jonalist kamarki tsoro har haka?" Haka taji sautin muryansa ya daki ƙirjinta. Saidai babu halin ta kuma wata maganar don me makakon taji afwa saima sake tsanani da jikin nata ya sake yi. Wanda hakan ne ya tilas tashi fita a room ɗin babu jimawa sai gashi ya dawo hannunsa riƙe da first aidbox. Ruwan allurai ya haɗa tana kwance a inda ya kwantar da ita se oum dake zaune a gefenta wacce fitarsa data gani ne ya sanyata shigowa. Allurarn ya mata yana gama mata ya fice bayan ya nunama oum yadda zata bata magungunan. Anan ɗakin tayi jinyarta har wajen 3 days abinta shikuwa Ak tun daga ranar be sake ko waiwayar inda take ba. Alhamdulillah jikin nata kuma yayi sauƙi sosea se atishawar da take fama kuma. Shi yasa kullum zaka taddata riƙe da tishu a hannu, Tafiyace ta gama Ak ta gaggawa zuwa ƙasar Swizland. ganin kuma yanayin jikin Alhamdulillah hakan ne ya bashi ƙwarin gwiwar tafiyan. Kafff gidan babu wanda yasan da tafiyar nashi idan ka ɗauke oum kawai don ko jesrah bata sani ba bare meerah wacce take ta kanta. dake ma ba wani daɗewa zeyi ba 1 week ne kawai zeyi ya dawo. ★ Today is just like any other day, karar alarm ɗin dana seta ne ya tadani ƙarfe biyar daidai kamar yadda na saba. Ban tashi ba illa mistike idanuna danay tareda addu’an tashi a barci ina haɗawa da salati. Sosae nakejin Though abubuwa sunyi min yawa amma bana raba ɗayan biyun harda maganganun danaji wanda na tabbata sune suke sake relax nawa tight. Yau a ɗakinmu na kwana tare da jesrah kallon bed ɗin da take kwance nayi har zan tada ta na tuna tana fashin sallah tuna hakan danay ne ya sani fasa tashin nata. Jiki a mace na miƙe tare da shigewa bathroom tsarki nayi tare da ɗauro alwula na kalli alkibla. ★ _SWIZLAND_ Katafaren two storey building gida ne mai matukar kyau da tsada iya haɗuwa gidan nan ya haɗu kai da ganin gidan kasan masu rayuwa cikin wan nan gidan ko dai wani babban ƙusa ne wanda yaci yasha harya tada kai. ko wani babban ɗan kasuwa gate ɗin gidan kawai abin a tsaya a kalla ne ɓangaren biyu ne a cikin gidan ga wani ɗan madai dai cin pool a tsakar harabar gidan, daga gefen hagu katafaren parking space ne mai ɗauke da katon rumfa da suke ɗauke da wasu shegun manyan motoci kusan kala biyar a wajen ƙirar *Mercedes-Benz* *McLaren solus GT.* *Roll (R) Royce boat Tail* *Bugatti* *Gtf cruiser land* motocin kawai abun kallo ne daga gefen dama kuma shuke shuken fulawowi ne awajen masu matiƙar kyau da ban sha'awa launin ja da yellow daga ɗan gefen parking space wani Katafaren wajen hutawa ne dake kewaye da glass wajen ɗauke yake da wasu fitattun kujeru masu numfashi set ɗaya launin sky blue a tsakiyar kujerun kuma wani haɗaɗen sofa table ne mai ɗan girma a wajen da gefe guda kuma ga wani katon deep freeze a wajen dake ɗauke da lemukan sha kai ko ta ina gidan nan Ƙarshe ne ya haɗu ba karya. Daga cikin gidan kuwa wani dankaramin terrace ne wanda kai tsaye mutum yake iya hango unguwar da motoci a bakin titi da kuma kai kawon jama’a tsilli tsilli. Wanda Wurin akwai taga mai girma a wajen da ke rufe cikin farin kyakkyawan labule terrace ɗin na ɗauke da doguwar kujerar hutawa (sofa) ta zaman shan iska, Se wani Ƙaramin table na glass a gabanta wanda koda yaushe za ka same shi cike da kayan marmari cikin dankaramin basket babu dare babu rana. Se gymnasium daga gefen wajen wanda yane shaƙe da kayan motsa jiki babu abinda babu kama daga nayi a zaune, a tsaye, a kwance, daga rigingine, na gudu. Duka dai babu nau'in da babu. Anguwar _ISLAMABAD_ kenan Ƙerarriyar anguwa wacce take cikin jerin rukunin mangan anguwannin birnin Swizland kena. Anguwace da duka tsarinta yake na manha masu ji da gidan rana wato (NERA, DOLA da HIROF) Wacce baki ɗaya jerin rukunin gidajen irinsu ɗaya ne daga waje sai daga cikine abubuwa suke banbanta. Wanda acan ne manyan ƴan siyasarmu ke barar da kuɗin su ta hanyar kama irin manyan anguwannin wasu ma kuwa siye gidan suke kai tsaye. Wanda inda kuɗin zasuzo su baza bana a tamu ƙasar da talauci beyi zurfi da ƙarfi har haka ba amma rashin kishin kai da suna lallai su ɗin wasu shegune a ƙasar suke fita yawon outing Manyan kasashen wajen suyi Challing abinsu. ★ A ★ K★ Tsaye yake ya ɗan rankwafa daga saman terrace ɗin yana kallon duk wani shige da fice na manyan motoci dama ƙananunsu. Sanye yake cikin wasu guntayen ƙananun kaya kansa babu komai sema gashin kansa daya baje wata har tana zubowa da saman goshinsa. Kana ganinsa ba indiye sakk hannunsa riƙe yake da wani glass cup wanda pineapple juice ke ciki yana sipping a hankali. Idanunsa a lumshe yake kunnensa manne da bluthoot yana bada jar danja da ƙoriya. Wanda hakan kai tsaye ke nuni da cewar waya ce yake ko kuma yanajin music ne. Ware manyan idanuwansa yayi a bazata maganar da aka faɗa may na sake bugun ƙirjinsa amma sammm hakan be nuna ahalaman hakan a tattare dashi ba. _KUWAIT_ *BY AMMEY LAYLERH* (Mirrah) *🦅 MIKIYA 🦅* _A wonderful world & Special anti terroRism squad_ ____________________ *MARYAM NASEER MIRRAH* ~AMMEY LAYLERH ✍️~ ✯ *~🌠 JAJIRTATTU WRITER'S ASS.... 💫~* BOOK Two…………………………񆬍✍ 21&22 _MEERAH_ A loƙacin dana buɗi ido na gama tabbatar da AK shine mijin da aka ɗauramin aure dashi na ci alwashin sai nayi sanadiyyar rugujewar rayuwarsa gaba ɗaya. Saidai ashe lamarin ba haka yake ba mutumin da akema kallon ɗan ta'adda ya rikiɗene wa al'umma duk da kasancewar shiɗin ba haifaffen nigeria ba. Mutumin da zuciyarsa take a tsarkake kallum kwanan duniya yana yin sane cike da tarin yaga ko wacce al'umma bata cikin matsala. Mutum na farko kenan dana fara ganin irinsa me wankakkiyar zuciyar da babu algus a cikinta, Mutum ne wanda kai tsaye zamu iya ƙiransa da me zuciyar zinare koma nace lu'u lu'u ko zarce haka. Tun daga loƙacin dana gama fuskantan komai shi kansa na gama fahimtar rayuwarsa abar tambayace don cike take da tarin sarƙaƙiya wanda badan tsayayyar zuciyar da yake da ita ba wanda da wannan tsayayyiyar zuciyar ne yama ƴan uwansa katanga ga dukkan tarin ƙalubalen dake fuskan tosu. Wanda da ace zuciyar ba a dake take ba da anjima da kaita ƙass anyi dumumu da ita kai tsaye. A ranar dana gama tabbatarma kaine cewar ehhhhhhh lallae shiɗin abin a tausaya masa ne a wata rana a wani dare dare mafi tsananin duhu wanda magauta sukayi amfani da loƙacin don son cikon muradinsu amma dake babu haƙƙin kowa a kansa sai Allah ya sauya musu mugun nufinsu ta hanyar katangar da Allah ya gina tsakaninsa da zina. _A Ranar A kuma loƙacin_ ★♡♡♡ A hankali Iskan ke kaɗawa gwanin birgewa yanayin weather'n garin gwanin ban sha'awa me cike da dadɗan yanayi. ga yanayin garin da hadari yama samaniya ado ta hanyar mata ƙawanya a hankali a hankali iskan ke kaɗawa me tafe da ƙamshin ƙasa amma hakan bai hana kaji daɗin iskan dake kaɗawan ba, A hankali Ak ke tattako staircase yana saukowa jikin sa sanye da wando 3 Quiter blue da Sweaetshirt mai laushi mara nauyi fara ƙal kamar Auduga. Se ɗaukar ido take tamkar yanzu ne ya fito da ita daga cikin kwalin ta saboda haske Se ya ɗaura danim jacket blue color mai ɗan girma a saman farar rigan, hannun sa na ɗaure da tsadaddar gold watch mai bala'in kyau da tsada sai kyalli yake yana ɗaukan ido, ya haɗe kyakyawan dogon gashin san nan nashi daya sha gyara ya ɗaure a can ƙarshen ƙeyarsa sai wani daya zubo kaɗan ta gaban goshin sa kamar mace, fuskar nan a ɗaure tam kai da ganin sa kaga Lion ɗin ne da gaske don yaci a ƙirasa da gargalion ɗin. Tafiya yake cikin majestical takunsa na isa da kuma izza kai tsaye dining room nashi ya nufa, jigba jibgan Bodyguard nashi zagaye da ploor'n har zuwa dining area ɗin. sanye suke cikin suit baki da glass baki a face nasu fuskar nan tasu kamar hadari a ɗaure tamau babu alaman imani ko ɗigo a ransu, sun jeru yali gefe da gefe sun sanya table ɗin a tsakiyar su sunyi ma wurin zobe. Tun AK bai iso wajen ba suka fara sara masa ko kallon in da suke bai yi ba ya nufi saman kujerar table ɗin, a sukwane ɗaya daga cikin bodyguard ɗin ya ja masa kujerar baya. Zaune yakai yana crosing ƙafarsa ɗaya akan ɗaya haɗi da ɗakilar woyansa. Da hannu yama ɗaya daga cikinsu nuni da Wata luxury warmer's me ɗauke da Hot Grilled chicken, nan take ya fara serving na shi tare da tura may gabansa. A nutse yayi cheak upp na cikinsa yana miƙewa tsaye bayan wanke hannunsa dan ba ɗabi'ar sabace cin ko wanne irin abinci da spoon. A nutse ya bar wurin drectly yana me nufar garden nashi ta kebantacciyar hanyarsa. ★ A nutse take durfafar garden ɗin yanayin wajen na sake burgeta sosae musamman yadda yake samun kyakkyawar kulawa. Sanya ƙafafunta kenan sautin muryarsa shine abu na farko daya fara ziyartar kunnenta,kafin daga bisani idanunta su sauƙa a kansa,dai dai loƙacin da shima ɗan motsin da yaji ya sakashi ɗaga kai idanunsu suka sarƙe wari ɗaya,yana daga tsaye dan shigowarsa kenan shima hannunsa guda ɗaya cikin aljihunsa ɗayan kuma mug ne na tea party dabai gama sha yana sipping nashi a hankali.... Wani kallo ya wurga mata ganin yadda ta kafeshi da mayun idanunta. Bakinta ta murguɗa may tare dajan ƙaramin tsaki tana ɗauke kanta a kallonsa. Chakkk ya tsaya da sipping tea ɗin dayay niyar yi.Lumshe idanunsa a nutse yayi yana jin wani irin bacin rai na taso may,idan har dai dai kunnuwansa suka jiye masa kamar sautin tsaki ya jiyo wanda yaga alamun fitarsa daga ɗan ƙaramin bakinta data turoshi gaba loƙacin da take hada sautukan tsakin. Ba tare da tayi aune ko tunanin hakan ba kawai sai ganinsa tayi gabanta yana binta da wani irin kallon data kasa gane masa. Haka kawai taji gabanta yayi mummunar faɗuwa kowanne sashe na jikinta yayi sanyi saboda yadda ya zuba mata mayatattun idanunsa,yana jifanta da wannan kallon da har ayau bata san ma'anarsa ba. Numfashinta ne ya soma ƙoƙarin sezing ganin irin kallon da yake binta dashi ga kuma daf da daf ɗin da sukay ya mugun takura mata. Sake waiwayowa tayi still har yanzu ita yake kalla kallon dake sake tunatar mata farkon ganinta dashi. Sake janye idanun nata tayi ta maida dubanta wani wajen daban, gaba ɗaya kallon da yake mata ya wuce ƙa'idar da jarumtarta zata iya ɗauka uwa uba kuma shirin rikicewa takeyi gaba ɗaya,saboda yadda tsananin kwarjininsa yake sake cikata. Da wani irin hanzari ta nufi hanyar barin garden ɗin da zummar fita,amma kuma kafin ta isa har ya isa ya tare hanyar ya kuma sake tsareta da shegun idanunsan nan. ★ "Wa kika ma tsaki?" Ya jefe mata tambayar kansa tsaye cikin izza da ƙasaitarsa "Ta yadda makaran kunnuwanka suka jiye maka yanzun ma se su baka amsarka!" kai tsaye ta jefa masa amsar tambayar bayan ta ɗauke kallonta daga gareshi. "Ko?" Ya faɗi wani shegen murmushin gefen baki na subce masa, Na irin mamakin yadda take iya jefanshi da duk wata maganar da tazo bakinta. Amma kuma ba abin mamaki bane idan yay duba da yadda ta mu'amulanceshi a gidan jaridarsu. Da yanda duk wata haɗuwa tasu basa taba wanyewa lafiya seta jefeshi da duk maganar da yazo bakinta .Fuskanta yake duba yanason gano daga inda ta samo wannan qwarin gwiwar Kyatt take iya tsaiwa a gabansa ta gwada masa rashin kunya,yayi imanin har zuwa yanzun bata gama sanin ko waye shi. Amma a yadda ya lura akwai ƙuruciya sosai tattare da ita Idan yace zai punishment nata ɗan ƙaramin abu kawai zaiyi da zai bata zazzafan warning,ta yadda ba zata sake marmarin maida masa martanin ko wacce iriyar magana bace nan gaba. ★ Ganin abinda yake shirin aikata mata ne ya sanya ta fakar idonsa ta tunkuɗi mug dake hannunsa a taje tea ɗin ya bare masa a jiki. Ita kuma ta ranta ana kare tana barin duka garden ɗin. Dake yanzu kamar ya zame min izini saina shiga sasaan Moh da kuma Umaymah haka kai tsaye na biya ta duka passess nasu. Tsaye naga Yasmine wacce nake ma fuskan kallon kamar na taba gani kodai na taba saninta. Kuma tunda tazo gidan so biyu muka haɗu sammm yarinyar bata da ɗabi'u masu kyau, kodan dama haka gidan yake ohon musu dai can ta matse musu. "Ki tabbar a daren yau yasha wannan lemon! Don shine kaɗai hope namu akansa na tabbata duk inda yakai ga kamewarsa da wani jiji dakai nasa wannan karon dole yazo hannu. Ni kuma daga loƙacin da kika tabbar min da yasha daga loƙacin nawa aikin ze fara bayan lafawan komai. Kana kin tabbata kinsha duk abubuwan nan dana baki kana bana da buƙatar koda Dada'nki ne ya san da wannan shirin namu Akan Wannan shegen yaro" Daga nan idona ya fara ganin bibbiyu ina tunanin su kuma waɗan nan mutanen har abada a haka zasu ƙare kenan a ya won tuggu da cutatar da mutane. (Ko wanne me tsautsayin ne wannan!) Na Faɗi a raina " Koma waye ubangiji karya baku nasara akansa" na faɗi a bayyane ina barin bangaren zafi biyu na haɗe min a loƙaci guda. Lallai wannan gida se adda'a kowa babu alkairi a zuciyarsa. Maganganun waccan ranar ne suka shiga dawo min turyan turyan. Rasss naji gabana yayi wani irin mummunan bugu inajin zuciyata na dunƙulemin wuri guda. "AK" na ambata a bayyane don ranar ma akan shi ne naji duka maganganunsu. "Tabbas shine" na sake faɗi inajin yanayin bugun numfashina na sauyawa daga matakin da yake zuwa wani matakin na daban. "Ya rabb karka baya waɗan nan mutane cutatar da wannan bawan naka!" Kawai se tsintar bakina nayi yana me wannan adda'ar. Gaba ɗaya yanzun kam shi kansa tausayi yake bani don yaci a taisaya masan amma shi girman kai da zafin kansa bazai taba bari ya fuskanci hakan ba. Haka na koma sashin oum suƙuƙu har yanayina yana kasa boyuwa na halinda da nake a ciki. Wanda hakan ya kasa boyuwa har oum take tambayana ko lafiya, amsa na bata da cewar lfy lou nake kawai dai banjin daɗin jikinane. Kwanciya nayi babu abinda ke tada ni in banda sallar da nake tashi yi. Haka har akayi sallan isha'i wanka nayi na zira riga da wanda na bacci masu ɗan kauri wandon ba dogo bane caan haka ba rigar. Babu daɗewa da kwanciyana oum ta shigo hannunta riƙe da Tea plask, "Doter te maka kibi min Garga da wannan duk yau ban jishi ba tun fitansa na safe" ta faɗi tana bani tea plask ɗin. gabanane naji yay mummunan bugu sanin cewar mutum ɗayane take ƙiransa da garga ɗin kuwa wato *AK* jiki babu kwari na miƙe tare da ɗora after dress akan kayan baccin dake jikina. Seda naje har bakin ƙofa jesrah ta tsayar dani ban tashi aune ba sai ji nayi tana feshe ko ina na jikima da turare. Bige hannun nayi ina faɗin "Banson iskanci fa jesrah miye kikeyi haka?" na tambayeta ina janye kwace jikina. "Gaskiyace wa yace miki ana zuwa wurin miji haka sikaukau babu ko ɗan kamshi haka? Kefa nama fahimta nine da kaine zan zaunar dake na koya miki darussan dake cikin aure, irin yadda ake mallake zuciyar mijin nan yaji duk duniya babu macen da takai mace a gareshi inba ke ɗin nan ba. Jeki dawo wllh daga yau zamu fara sabon darasi don da gasken gaske so nake ki mallaki Akiey ta yadda wannan ɗan banzan zafin kan nashi ze ragu" "Ban haya na wuce jesrah tunda shirmene a gabanki ke" na faɗi ina ƙoƙarin rabata na wuce. "Da gaske so nake ki zama cikakkiyar matarsa Meerah" Banko sake waiwayota ba duk kuwa da cewar inajin maganganun shirmenta. Duk inda na keta na wuce se kaga hadimai na rusunar da kawunansu ƙasa wanda hakan samm ni baya min daɗi baki ɗaya. Sedai babu yadda na iya tunda suka san matsayina a gidan kuwa, duk taku ɗaya da zanyi ina jinsa ne tare da bugun zuciyata. Rass gabana ya bada sautin bugu loƙacin da na kusa cin karo dashi, baya nayi zan faɗi yay saurin taroni ina komawa saman jikinsa. Zafi rau ɗin da naji a jikinsa ne ya sanyi saurin janye jikina a nashi tea ɗin na ajje masa a wurin ina faɗin "Ganan inji oum" na juya da nufin komawa ko taku ɗaya banyiba naji sauƙar hannuwansa ƙan ƙuguna abinda bai taba faruwa dani ba yazo min kuma a bazata. "Don Allah ka sake ni miye hakan ni banso!" na faɗi a rarrabe zuciyata na bugawa sosae. Bai amsa min ba saima wani lumshe idanunsa da yay yana matse fuska alamar da abinda ke damunsa. Gabana ne ya faɗi tunowa danai da wancan maganganun nasu umaymah zance koma na Moh jiddo. A take kaina ya shiga juyawa inajin wannan karon bugun da zuciyata kemin ya zarta ka'idarsa, don kai tsaye maganganun mutane biyun nan ne sukai tasiri a cikin zuciya. Ita moh jiddoh kai tsaye paisoning nashi tasa ayi ɗaya daga cikin hadimansu mash kula da bangaren kitchen, ita kuma umaymah table desire zasu sa may don ya kusanci ƴarta don cika muradinsu. (Wan ne ne daga ciki kenan?) na faɗi a cikin zuciyata. Haka kuma cikin suɓutar baki na furta "Baka da lafiya ne?"    Maimakon ya amsamin tambayana sai ma ya wani lumshe idanunsa da matso da fuskarsa kan tawa sosai. Idanuna na runtse da sauri ina ƙanƙame jikina tare da kauda fuskar tawa gefe. Sai kawai naji saukar numfashinsa akan wuyana zuwa ƙasan wuyan nawa da cikin kunnen yana shinshinata can kuma kamar wanda aka tsiƙara se jinay ya ɗaukeni cilak yana fita dani gaba ɗaya daga ɓangarenma baki ɗaya. Ta wata sihirtacciyar hanya yabi wanda take kamar irin ginin nan na ƙasa. Abin mamaki se gamu a wani plat na daban kuma wai duka anan cikin ɓangaren nashi muke nefa. Tafiya ya shiga yi dani jikinsa na sake ɗaukan zafi wanda na take da tabbacin badan taurin zuciya irin tashi ba da seadai ace ko yana kwance a gadon asibitne ko kuwa dai shima memar irin hakan hake da buƙata a dai irin wannan halin. A ɗaya daga cikin manyan bedroom na plat ɗin ya shige damu akan wata farar sofa ya zaunar dani yana fesar da numfashi me zafi. Cikin ƙarfin hali yayi amfani da landline na room ɗin maganar second yayi yay ya janye wayar a kunnensa. Kamar ten minutes ya sake ɗaukana ya fita damu compound na plat ɗin nidai se aikin rarraba ido kawa nake don shine nawa. cikin wata lafiyayyar mota blue black ya sanyani shima ya zaga yana komawa mazaunin driver. Babu kowa a harabar wurin da dukkan alamu kuma babu me rayuwa a wurin dama. Revarsw na car ɗin yayi tare dajanta da wani kalan mugun gudu na tsiya,wanda hakan ya firgitani ido na rumtse da ƙarfi har bansan sanda na ɗamki ɗamtsen hannunsa. wanda ni kai tsaye    bansan hakan abinda ya haddasa masa. Wani kalan jan burki yayi harda saida kaina ya daku da sterring na motan. Shi kuma wani kalan rumtse idonsa yayi don ji yayi a loƙacin saura kaɗan numgashinsa ya rabu da gangar jikinsa. Sake dakar haban motar yayi yana sake bata wuta ko kallon gabansa baiyi, kai tsaye a hadadden gidansa dake _MASHATLE SHUWAIK_ ya taka wani kalan wawan birki. Take motan yayi da balain ƙarfin tsiya cikin kiftar ido da buɗewa na'ura ta tantanceshi. A compound na get ɗin ƙarshe ya taka birki. Ƙafofina na zubo ƙasa da niyar fitowa se jinai anyi sama dani tare da tafiya dani a nutse cikin yanayinsa na kamewa. Ta wata ƙofar glass yabi damu sai gamu a wani ƙayataccen bedroom. Jikinsa kuma    zuwa loƙacin ya sake ɗaukar ɗumi sosae.    A zabure na mike ganin yadda loƙaci guda yanayinsa ya sanja baki ɗaya. Hannuna ya kama tareda janyoni na faɗa saman kansa daman already ya rigada ya zauna saman sofa. Kan ƙafafunsa na faɗa ya haɗeni da zazzan jikinsa yana rungumeni gaba ɗaya na.A hankali ya ciro da shuɗaɗɗun idanuwansa kaina yana me bina da Wani kalan kallo me nakasta gangar jiki. Faɗuwa gabana yayi na ɗago na sake kallonsa a karo na biyu ganin irin kallan da yake min yasha banban da waɗan can na baya. kafin na sake wani yunƙurin tuni ya sake matseni a cikinsa sosai akan gafafun nasa mukai kyakyawan haɗewa muna fuskantan juna kirjinmu a haɗe. Yadda yake jin bugawan zuciyata ne yasake gigita tinaninsa ya zagayota da hannuwansa Yana saka Kansa cikin wuyana yana Jan numfashi me ƙarfin gaske, Wanda ya sake bugarmin da zuciya da ƙarfi hakama numfashinsa me dumi yake sauƙa akan fatan wuyana tini suka tayar da tsigan jikina. "Wayyo ni Allah na shiga uku! dan Allah Yaya *AK KUWAIT* ka rufa min asiri ka ƙyaleni, wai minene haka kake yimin kamar wani maye" Na faɗa cikin yunƙurin miƙewa da ɗan sauran ƙarfin daya rage min. Gocewa yay daga kyakykyawar rungumar da yay min ya koma gefena. ɗaukana yayi chakk yana shigewa dani wani irin rantsatstsen bedroom na alfarma. Kwantar dani yay cikin wani irin muryan da ban taɓa jinsa dashi ba ya ɗora bakinsa kan kunne na tare da furta. "Idan na rufa miki asirin ni kuma wazai rufa nawa _MIFRAH_?.       Yanda ya ambaci sunan nawa cikin wani irin salon daya bugarmin da zuciya.       "Pls ki tsaya idan kika bi a sannu komai zefi xuwar mana da sauƙi" Ƙoƙarin kwace jikina nake tare da furta "Don Allah nidai ka ƙyaleni karka cutar dani kawai ka medani wurin oummu tare d jesra ma yafi" "Zan fiki cutuwa idan nayi hakan *MIFRAH!* pls relax beb" Ya faɗa cikin muryar data sake firgitani sosae. Kici kicin kwatar kaina na shiga jin al'amarin na neman fin ƙarfina. Sake matseni yay a jikinsa dake kakkarwa sosae buɗe min rinannun idonsa yai duka wanda na lura baya son na kalla aikuwa sake rikice masa nai ina faɗin ya sake ni bana so. "Tun wuri ma kara ki tsaya ki nutsu dan wannan abin naki bashi zai hana faruwar komai ba dan ina da taurin kai, idan har nace zanyi abu ko menene shi to kuwa tabbas zanyin. Idan nace bazan ba to kuwa ko mene zai faru sedai ya faru don haka ki nutsu pls!!" Ya ƙare maganar da rufe min baki da nasa daga haka bai sake bani wata dama ba koda ta shaƙar numfashi ne cikin sauƙi. Gaba ɗaya seya sanja daga ainihin AK da kuka sani xuwa wani AK ɗin na daban. Babu tsammani kuma naji ya zare lips nashi a nawa tare da kama rigar jikina tun daga sama har ƙasa yana rabata gida biyu. Dama after dress anbar maganarta tunda a kan sofa. Take ya saki Wani mahaukacin numfashi ganin lafiyayyan suran jikina a bayyane. Tashi rigar ya raba gida biyu shima kafin ya janyoni yana sake haɗe bakinmu cikin sanyi ƙirjinmu na haɗewa wuri guda. Saura ƙiris ya rasa numfashi da bugawan zuciyarsa akan yadda fatar jikinmu da babu kaya ta haɗe. Sabi da yanda kirjina da ba kaya ya sauƙa kan nasa kirjin ba kaya ajiki Shima. A yanda yakejin kansa har wani turiri turirin hayaƙi na fita bazai iya cigaba da haƙuri da hakan ba. Dan haka ya ɗagoni yana bina da wannan mayen kallan cikin idanuwan dagyar ya iya furta "I need you MIFRAH" ya furta yana bina da wani irin french kiss Kaman zai cinyeni ɗanya. A kirjina zuwa bayana da marata ya ringa yawo da hannunsa cikin wani irin Abu da yake jin kaman zai fasa Kansa. Kashe wuyana yahau Yi da harshensa zuwa ƙirjina wanda kai tsaye hakan ya nemi daya sumar dani sabi da wani abune dabai taɓa faruwa dani ba. Shi kuwa Kansa tini ya juye notikan Kansa suka kunce ya rasa control nashi baki ɗaya Yana son yay romancing nata dakyau Amma wutar abinda ke ruruwa a tsakar kansa taci karfin hakan. Duk wasu shure shuren da nake yine naji ya tsaya chakk jin abinda yake shirin aikatamin ko kafin nayi wani yunƙuri tuni harya ɗauki harama. ★ Tunda nake a rayuwata ban taɓa tunanin akwai makamancin irin wannan tashin hankalin na kana ji kana gani ba sai yau. Sam baya jin roƙo baya jin magiya. Saima sake tabbatar min da shi ɗin mayuncin zaki ne da in ya ɓalle abinda ya fito nema kawai yake farauta. Tun ina iya banbancewa har komai ya ƙwace min daga gangar jiki zuwa fitar numfashina. A wannan daren komai dazai faru ya fara rubuta kansa. A wannan daren kunɗin ƙaddarar wasu ya buɗe na wasu kuma ya rufe, A wannan daren me afkuwa ta afku wanda daren shine ya zamo silar warwarar wasu cukurkuɗaɗdun duhun daya daɗe da mamaye koda ƙyallin haskene. Sai gashi a dare ɗaya Allah yayi a rana ɗaya Allah ya kawo sauki cikin sauƙi me haɗe da wanko jurwayen dake gudu yana kwaranya a wasu zukatan. Ya kuma toshe duk wata hanya ta datti me ɗauda wacce ingancinta be kai ba. Ya kuma bayyana hasalin *GARKUWAR GANI NA WANNAN MASARAUTA.* _JADDERN ASHAAN_ To ai shikenan a gimtse kawai. 👋Hannu kamar ze cire gadon baya kamar ya ɓalle kai wllh typing? Typing azabane. *Don girman Allah Idan baki biya ba karki karanta min littafi don idan nayi Allah ya isa banyi laifi ba nake ganin?😕😕😕😡* Uhummmmmmm Taku *AMMEY LAYLERH* (Real Mirrah) *🦅 MIKIYA 🦅* _A wonderful world & Special anti terroRism squad_ ____________________ *MARYAM NASEER MIRRAH* ~AMMEY LAYLERH ✍️~ ✯ *~🌠 JAJIRTATTU WRITER'S ASS.... 💫~* BOOK Two…………………………񆬍✍ 23&24 # HOT LOVE # ROMANCE SCENE # DESTINED # LIFE # REVENGE # AK MEERAH # IDENTICAL TWINS (Hhhhhhhhhhhhh lalla i mafarki Shirmene jama'a daga rubutun littafin MIKIYA saiga AMMEY'nku nacin uban tanacin uban ƴan Nigeria harda su tada aljanu. Wllh da gaske mafarkin nayi😱😓😫 hardasu gwara kawuna Ohhhh Rabbi) ♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡ ★ _NIGERIA_ *Apapa lagos* Gyara zamansa Zubair tanbuwal yayi kafin kafin yaci gaba da faɗin. "Babban sojane da babu kamarsa duk wani soja da zaka kalla to shi ya zarta hakan don kuwa akaf cikin duniyar duk inda ya zaga yana da wani irin babban matsayi. Uwa uba kuma Akwai shi da wani irin kwarjini da farin jini ga kuɗi don wannan yaron tycoon ne me zaman kansa. ga mulki tarin masoya Allah ya bashi ga bala'in izza kafin yayi magana ya buɗi baki yana magana haka rakaka caff ashe kuwa za'a shekara sittin manya manyan gidan gidajen jaridu da tv da duk wata kafa ta sada zumunta nemansa suke ruwa a jallo don samun damar yin hira da shi kullum yana zagaye da jibga jibgan Bodyguards suna take masa baya ga wasu jibga jibgan sojoji a gefen sa! A takaice dai A MALEEK The Handsome of the world ne baki ɗaya mutumin daya kafa rishinan nan kasuwancinsa a ko ina a kowacce duniya. Mutumin da kake mutuwar haɗa hannun jari dashi wato (E) grouo ɗinan. Ba iyaka E group duka wani company da zaka ga yakai ya kawo to na EMAAR's MALEEK. mutumin da mutane suke mutuwar ƙauna fiye da numfashinsu ata dalilin kyautata musu bawai iyaka ningeria ba har dama sauran ƙasashe. kuma fa wai hakan ba ganin fuskar sa suke ba don kullum da facemark yake yawo ba abun da zaka kalla sai idon san nan me kama dana mage. shima idon time to time yake zama ba glass amma a haka jama'a ke mutuwar son sa musamman ma ƙasarnan tamu, yana yin bad da kama don mu'amulantar mutane daban daban. Shaharren ɗan kasuwane dayay shura a cikin duniyarmu ya kuma kasance tamkar ƙashin bayane wa talaka ya buɗe gidajen marayu a kowacce duniya. Yana zamar da marayu tamkar ƴaƴansa ƙannansa yanzu haka labarin da nake baku kusan duka yaransa marayune wanda ya inganta rayuwarsu! Su kuma suka zama bodygurds nashi don sunce rayuwarsu fansa ce a gareshi. Ba kowa bane wannan EMAAR's ɗin se wannan wanda muke kalla a matsayin tantiri wanda dama son zuciyane ya sanya muke son ɓata may suna. Ance tunda yake a rayuwarsa duk yawon kasashen da yake wani media trend be taɓa fira dashi muraran ko ganin face full nashi ba se ita wannan shahararriyar ƴar jaridar tamu _MARYAM ABDULLAHI GWANI_ wace itama daga karshe kakansa sarkin kano ya aure masa ita. Ashe ita kanta yarinyar jikar Sarki Ash Mayesh ce way anyima mahaifiyarta kucciyane tun tana yarinya a cikin masarautar EMAAR's akan mulki, ashe kuma bama ƴarsa bace yanzu haka Sarki Ash mayesh yana nan a cikin garin nan a gobe ma jirginsa ze tashi tare da Ƴarsa don taga dangi kaji fa yadda Allah yake ikonsa. Wllh a loƙacin da Governor Ibrahim Khaleel Nasara yake bani labarin nan yadda kasan nayi fitsari a wando haka naji. Wllh Da idona naga Sarki Ash sarki me daraja sarkin Madina" Tunda Zubair tanbuwal ya soma magana wurin yay kamar ruwan ya shanye. Cikin rashin rashin haƙuri da ƙawa zuci da kuma dama shima zuciyarsa a tafashe take Isa manu ya furta "Duk akan waye kake uban kurawanne ne kana ehhhhhhhh ƙaunata a duniya naga na haɗa hannun jari da (E) group INVESTMENT amma banda yanzun da nasan waye hasalin me company'n!" Isa manu ya faɗi yana ɗauke kansa dake balain sara may. "AK shine hasalin me company,n" "Aaaaaaa meeeeee?" Duka har suna rigan haɗe baki wajen tambayar hakan. Banda Isa manu da dama tun tuni Reza ya sanar dashi kuma tun daga loƙacin be sake sanya Reza a cikin idanunsaba, "Wai mi yasa duka rayukanmu suke watangaririya a hannun wannan shegen yaron ne iyeeee? In taƙamarmu kuɗi ya fimu,in taƙamarmu iko,mulki,power, duka ya fimu meya mana saura? Meya rage mana kuma shi kansa A...K...K ɗin nasan ba tsira zeyi ba daga tarkonsa" Audu bashasha ya faɗi cikin kunan rai don shi a yanzu babban abinda yafi buƙata shine yaronsa kawai. "Kenan dai dama duka zaman akan shine? To miye amfanin hakan duk dai akan mutum ɗaya ne ake wannan abin wato _ÊÃGLÉ ÆK?_" Isah manu ya sake faɗi donshi yanzu aduniya abinda ya tsana yaji ana ambata shine koda me irin wannan sunan ne. "Dole sunansa kawai abin girgizawa ne Manu don se yanzu brain nawa tayo min zeroying mind nawa tabbas shine yayi kiddnaping namu nida nida me girma gwamna a loƙacin muna tsaka da wata magana me muhimmanci" Zubair tanbuwal ya faɗi yana miƙewa tsaye hannuwansa goye a bayansa yana aikin safa da marwa. "Duka ba wannan ba tunda dai duk wannan sun riga da sun wuce magana ake ta ran ƴaƴanmu dake cikin hatsari ANCE MONEY IS POWER! Shin kun yarda? Ance kuɗi kan iya maganin komi har cuta da baƙin ciki dama damuwa me yasa yanzu kuɗaɗen namu basu mana ba? Kunga kenan kuɗi ba maganin komai yake iya yiba tunda be temaki ƴaƴanmu ba mutane da yawa suna cewa kuɗi kan iya siyan kowa shin me yasa ya gaza fansar ran yaronmu dake cikin hatsari a maban banta wurare" Audu bashasha ya faɗi shima yana miƙewa tsayen zufa na karyako masa. "Amma duk da haka ba zama zamuyi zaman zuba ido ba dole wani option ɗin zamu ɗauka na salon kare kai bawai zamu tsaya muyi folding hands namu muna kallonshi in pains ba. Na shirya ma hakan dama tun tuni bara ku gani" ya faɗi yana zaro tamfatsetsiyar wayarsa a cikin aljihunsa kai tsaye waya yayi ta second dabe wuce five ba ya datse ƙiran,wasu kattan maza ne majiya ƙarfi suka shigo palon su shida suna sanye da riguna da wando baƙaƙe da tie kaman masu aikin bank. Fuskansu baƙaƙe wulik kamar irin kafiran farkon ƙarnin nan baƙar fuskarsu se ƙyallin man shafa take idonsu ranbaɗaɗau da farin kwalli irin wanda ake sama jarirai sabuwan aihuwa. "JESKA, MALIAN'S ,HIRITHIKROSHAN ,ARIAN, TIGERSHIROF. Waɗan nan wasu gogaggun Masheƙane wanda na tabbar idan suka kama AK saidai uwarsa ta haifi wani don tasa tazo ƙarshe" ya faɗi tare da kallon samudawan mazan cikin son nuna gwaninta da bajintarsa ya furta. "My Hero's kun shirya shiga farautar AK _ÊÃGLÉ ÆK?" "Ye's sir." Suka haɗe bakunansu tare da cira ƙafa su doka ƙasa. Aikuwa ya burge ɗin dan duka fuskokinsu take suka washe koya najin kamar anyi an gama ne an gama da rayuwar AK. "Amma dai ba iyaka su kenan ba?" zubair tanbuwal yayi tambayar "ehhhhhh ko wanne daka gani anan yana da rundunarsa guda su duka shidan kuwa" ajiyar zuciya zubair T ya saki yana faɗin. "Haba koda naji don wllh yaron nan kullum tafe yake da nasa ƙartin majiya ƙarfi barin ma wasu biyu da duk inda ze shiga ya fita suna nanike dashi. A yanda naji sunji rayuwarsu tamkar rayuwar Ak ce dole kafin wani mahaluƙi ya sama zarrar taɓashi akwai buƙatar ya fara kawar dasu tukunna gasu da shegen ƙarfi kamar dutsen dala" Daga nan suka shiga nunnama mazan nan duk irin tsarin da suke son komai ya tafi. Daga nan suka sallamesu bayan ko wannensu an bashi kafin alƙalami na wasu maƙudan kuɗaɗen da idan kuka jisu sai sun firgita wasu zukatan, tare da file da komai ke rubuce a cike. Daga nan suma suka sake tattaunawa sama sama da haka zaman nasu ya tashi. ★ _KUWAIT_ Wata irin wuta AK yaji kaman ta watse cikin kansa tsaban abinda yaji din cikin fita hayyaci ya fizgota jikinsa yayi mata wata irin runguma Yana ƙankameta kaman zai ɓallata gida biyu wanda babu tan tama da ace a farke take babu abinda ze hana ta sake somewar a karo na biyu,sedai dama a sumen take tuni tabar wannan duniyar zuwa wata duniyar ta daban inda ta miƙata ga wani babban mataki wanda wannan alƙalamin na ƙaddarar ta ya sake rubutata cikin sabon babinsa na daban. Shi kansa somewan yake Neman yi a loƙacinda jikinsa ya sake sosai yana jin jikinsa dama kansa kamar ba wannan AK ɗin ba kamar ba Hasalin _ABDOUL-MALEEK HASSAN AL-HASSAN EMAAR's KUWAIT_ ba kamar ba wannan _GARGALION_ ɗin na oummun shiba. Ƙanƙameta sosae yayi kusan mintina nawa yana jin yadda numfashinsa ke barazana da barin gangar jikinsa. Wani zafin jikinsa ya sake ɗauka sosai fiye da farkon loƙacin da suka shigo koma yace tun loƙacin daya sha wanna pink lemu'n, wanda kai tsaye yasha oumm ce ta ajje may sedai ko motsi beyi b dag inda yake gaba ɗaya komai nashi ya tsaya da aiki chakkk. Wani mayen abu na bijiromasa tamkar ya mutu yake ji a loƙacin, wanda kai tsaye ya gama fahimtar komai don a take daga inda yake zaunen ya kunna nu'urarsa dake jikin systerm nashi wanda kai tsaye take naɗe masa komai dazai faru a palon nashi. Kamar daga sama yaga shigowan yasmine da sadda ta saɗaɗo cikin sanɗa ta ajje may lemu'n tana faɗawa wani bedroom na cikin palon. Babu jimawa kuwa se gata ta fito cikin wata ƴar iskar shiga a yadda tayi zata kuwa a hakan ta same shi. Ganin hankalinsa ya fara barin jikinsa ne ya sanyata babu tunanin kuwa ta faɗa jikinsa bayan ta fige rigar jikinta. Wata muguwar shaƙa yama wuyanta tare da buga kanta da jikin sofa, Cup na lemun ya janyo tare da matse bakinta ya juye mata duka be saketa ba seda ya tabbar ta haɗiye lemu'n duka.kana Idanunsa a kulle ya miƙe tsaye da ita yana tunkuɗata wani ɗakin horonsa me tsananin duhun tsiya yaja ƙofar ya kulle. Duk kuwa da yadda take kururwar ya temaka ya buɗeta amma kota kanta be biba, Ya juyo kenan da niyan fita kenan kuma sega Meerah kamar wacce aka tunkuɗo masa ita. Duk yadda wutar abinda aka sanya masa ke sake rura jinin jikinsa seda ya gama tantaceta kafin ya aro jarumtar tarota aloƙacin da tayi baya. Babu ɓata loƙacin komai ya sungumeta ya fita da ita, don ya tabbata idan harbe samawa kansa mafita na abinda ke azashi yana tada zaman lafiyarsa ba ze iya rasa rayuwarsa a yadda dai yake ji ɗin nan. Wata ijiyar zuciya ya sauƙe da ƙyar ya iya buɗe idanuwansa dake masa har wani kalan yaji yaji ya motsa hannunsa a kasalance ya janyeta daga jikinsa yana me kallan fuskanta datai wani irin ja sosai hawaye da majina sun cakude mata harta wuri gud harma sun bushe. Kafafunsa ya ziro ƙasan gadon ya miƙe tareda nufar bathroom ɗaure da towel. Wanka yayi da ruwa me zafi sosai saboda jikinsa ya sake sedai kwata kwata sake zafi jikinsa yayi haryana fidda hucin zafi sosai sabi da Wani irin zazzabi me ƙarfin gaske da yake sake rufesa take. Daƙyar ya iya dawo da kansa daƙin a galaɓaice. Kallonta yay da idanunsa da har yanzun yake jin basu dawo masa daidai ɗin suba. Gwada ɗaukarta yayi don ya taimaka mata seta hajijiya da jiri suka kayar dashi saman kanta. Wanda zafin jikinsa da kuma nauyin daya mata ya sata jan nimfashi kaɗan a wahalce. Kasa yi mata komai yayi saboda yanda jikinsa ke fidda zafi da rawa sosai ya sake yunƙurin gwada temaka matan sedai hakan be samu ba dole haƙura yayi daƙyar ya iya janyo wata rigarsa yazira mata. Cikin dauriya da danne zafi da ciwon dake sake nakasta jikinsa ya miƙe yana layi ya nufi landline na cikin bedroom ɗin ya saka ƙiran Hasken sa. Magana ya mata cikin wahala da fita hayyaci ta second uku kawai "Jadderh ki shigo bedroom nawa" daga haka ya datse ƙiran ita kuwa can jaddern Ashaan kai tsaye ta gane cewar yana cikin gidan kenan. babu ɓata loƙaci batai duba da uban daren daya tsala ba Kai tsaye ɗakin ta nufa. Tsananin duhun ɗakin ne ya sanyata lalubar makunnin haske ta kunna, yashe ta ganshi warwas a ƙasa gabantane ya faɗi da sauri tana nufar wurinsa A rude "Subhanallah shalelen haske baka da lafiyane? Meya faru dakai?" ta shiga tambayarsa a ruɗe ganin yadda jikinsa ke rawar ɗari yana fidda wani irin hucin zafi. "Ki fara temaka ta fisrt" ya faɗi a wahalce yana mata nuni da kan gadonsa. Rass Rass haka gabanta ya sake bugawa da sauri ta miƙe tana nufar kan saman gadon. Kwance ta ganta sanye da kayansa a jikinta kaman babu numfashi a jikinta ganin ko ina nata baya motsi. Da sauri ta ƙarasa gurinta tana ambatar "Ya Allah!" Bata hau gadon ba ta janyota tareda sauƙo da ita ƙasa a hankali itama jikinta na rawa. Wani mayen zafin da taji a jikinta tareda jinin data gani a ƙafafunta ya Sakata sake rikicewa a firgice ta kamata duk da bata iya dadaukanta duka ba. Ganin tana ta rasa yadda zatay da itane ya sanya shi tashi a mugun jigace yana temaka mata suka shigar da ita bathroom. Fita yayi da kanta ta haɗa ruwa me zafi sosai da sosai tana me sanya meerah ɗin a ciki. Azababben zafin daya ratsa tane ya sanyata buɗe kunburarrun da sukai jajir suka kumbura ba tare da ta motsaba sosai saboda batada ƙarfi ko kuzarin da take jin hannunta ma zata iya ɗagawa ba. Sema wasu siraran hawaye ne kawai da suka gangaro mata ta gefen idonta masu zafi suma. Hawayen tausayin meerah ɗin ne ya ciko idanuwan jaddern loƙacin da ta gama buɗeta ta duba taga mummunan aikin da Haskenta yayima meerah ɗin. "Da gaske kece hasken da zata kawo sauyi a cikin EMAAR's Maerayama" jadderh ta fadi bayan ta share kwallar tsananin tausayin meerah ɗin. Tsaf jadderh ta gyare meerah wanda ta gasata sosae.da taimakonta ta fito a kusa da inda yake kwance ta zaunar da ita. bedsheet ɗin gadon ta sanja musu da wani wancan kuma ta jefa musu cikin worshing machine, Meerah ɗin ta fara kama takai kan gadon kana shima ya koma ya kwanta fita tayi babu jimawa sai gata ta dawo hannunta riƙe da maganganu Ak ɗin ta bama tace ko wannensu yasha ita kuma ta fice tana ja musu ɗakin. sha yayi itama ya bata kasancewar bata da wani kataɓus ne ya sanya babu musu ta amsa tasha. Kwanciya suka sake yi lallausan farin duvet ɗin dake gefe yaja ya lulluɓesu bayan ya shigar da ita cikin jikinsa. Daf da asuba bacci ya ɗaukesa dan haka baima samu sallan ba sai ya tashi a makare. Idanuwansa ya shiga buɗewa a hankali batareda ya motsa ba sabo da tana a cikin jikinsa ne har yanzun. ɗumin numfashinta ne yake sauka a cikin wuyansa ahankali yana tayar da tsikan jikinsa ahankali. A wahalance ya ɗora idanuwansa da sukai nauyin baccin daya tashi da Kuma na mutuwan da jikinsa yayi yana kallan fuskanta dake bacci a natse ta shige jikinsa ta nade kaman baby. A natse ya janye jikinsa yana miƙewa tsaye a hankali bathroom ya shiga shawer ya fara sakarma kansa kafin ya ɗora da alwula. Anan cikin ɗakin yayi sallah bayan ya idarne ya dawo gabanta. Ɗaukarta yayi kaman wata baby ya nufi bayin da ita rasa yadda zeyi da itane ya sanya shi sakar musu ruwan ɗumi kawai yana kwantar da kanta cikin ƙirjinsa don gudun kada ruwa ya shigar mata ido da hanci. A bazata taji sauƙar ruwan don haka ta sake cusa kanta cikin jikinsa tana sauƙe ijiyar zuciya.wanka ya mata tare da ɗaura mata alwula yana naɗota cikin towel bayan ya gama mata komai, a gaban katon mirrow'n ɗakin ya zaunar da ita. Bata da wasu kayan dole ya samar mata wasu guntayen nashi ya zira mata shijjab ɗin daya tabbar na jadderh ne ya zira mata. Sake ɗaukarta yayi ya ajje ta akan sallaya, jikinta na rawa sosae ta tayar da sallar tana idarwa ta kwanta a wurin tea me zafi ya haɗa musu yana dawowa ɗakin. Jikinsa ya maida ta yana bata tea ɗin. Kawarta da kanta tayi wani hawayen na sake zubo mata. "Meyasa ba zaki sha tea ba? Do you want something?, Menene zakici? to na haɗa miki uyummmm?" Ya tambayeta cikin kulawan da ya sanyaya jikinta sosae. Zuba masa ido tayi tana kallan bakinsa dayake magana zuwa idonsa kai tsaye ba tare data bashi ko ɗaya tambayan da yake jefo mata ba. "Bana jin shan ne!" ta bashi amsa tana ƙoƙarin komawa kwancen, riƙota yayitare da dawota ita jikinsa daya cire rigan yana kwantar da kanta shima yana ɗora kansa saman nata daya kwantar. Like kiss ya sauƙar mata a kan goshinta yana miƙewa tsaye da ita yana komawa saman bed. Bacci sosae suka sha me rai da lafiya kasancewan zuwa yanxun babu zafin jikin. Ƙarfe 10:26 Ƙarar door beel ya farkan dashi. A kasalance ya shiga buɗe idanuwansa fararan sawayensa ya ziro yana miƙewa tsaye. Yana buɗe ƙofan yaga roboot ɗin Jadderh ne tsaye hannunsa riƙe da wormar's masu kyau guda biyu, amsa yayi yana rufe kofan ya koma ciki brush yayo be tasheta ba ganin baccinta take a natse. Kasancewar dama rabonshi da wani abincin kirki tun n jiya da rana ne ya sanya shi ɗanci sosae. Bedsheet ɗin nan ya shiga ya wanke da kansa motsin fitowar sane ya farkar da ita, Zaune tayi ƙoƙarin tashi sai kuma tayi saurin komawa tana runtse idonta da ƙarfin gaske. Wani shegen kukan da batay masa a daren jiya ba ta samu damar sakar may a yanxun. Goshinsa ya dafe tare da ambatar "Ya Rabb!" ƙarasa fitowa yay yana zama gefenta tare da ɗan shigar da ita jikinsa. Rigima sosae ta ɓalle masa dashi wacce ta nema haukata masa kai. Bakin rigimar ya toshe da nasa gaba ɗaya kawai don ya rasa ma yadda zeyi da ita ne kawai. Da haka ya kawo ƙarshen rigimar da kansa ya tsaya ya sake dubata. Ba ƙaramin tausayi ta bashi ba ganin kalan azaban daya bata a daren jiyan. Magungunan ya sake ɓalla mata ya bata tasha. Ruwan zafi ya sake haɗa mata ta gasa kanta sosae tare da wani magani ya haɗa mata. Tana fitowa kuwa taji dama dama sosae abincin ya zuba nata bata wani ci da yawaba ta ture, be takura mata ba ya ƙyaleta kwanciya ta koma shi kuma ya shiga aiki a laptop nashi. Wajen ƙarfe biyu ya kammala komai bathroom ya faɗa wanka yayo ya fito a shirye cikin fasion summer with hooded sleeveless da fcap din Calvin Klein blue sai face mask da bakin shade kai tsaye ya fito don samo mata kayayyakin sawa. A Wani babban mall dake ɗauke da sunan _A&Z malla yayi parking motansa bai shiga ba yana zaune daga cikin motan yayi amfani da wayarsa shopping ɗin komai dayake buƙatan yayi. Babu daɗewa aka fito dasu aka Saka masa a bayan motansa cikin wani irin girmamawa suka gama zuba may komai sw wani sara masa suke. ★ A can kuwa cikin EMAAR's sosae hankalin umaymah ya tashi ganin har wayewar gari babu yasmine babu halamarta, ga idan ta ƙira wayanta baya shiga swich off ne yake faɗa mata. Daga ɓangarensu oum ma hankalinta sosae yake a tashe ita da jesrah. Bayan gari ya gama wayewane jesrah taje take faɗa mata meerah fa ba tare da ita ta kwana ba. Hankalin Oum idan yayi dubu toya tashi, cikin tashin hankali ta nufi ɓangaren AK tunda tasan shine last fitanta. A kuma daidai wannan loƙacin itama umaymah ta isa ɓangaren Ak ɗin hankali tashe itama, a ƙofar shiga suka haɗu hakan yasa kowa yabi kowa da kallon tuhuma da tambaya. Shareta oum tayi tana faɗawa ploor'n ganin baya cikin palonne ya sanyata faɗawa bedroom nashi amma ba Ak ba meerah fitowanta yayi daidai da sanda umaymah ta ɗaga rigar yasmine tana fasa wani ihu me balain ƙarfi. "Shikenan ya lallata min rayuwar ƴata tunda ga rigarta nan yashe ai!" Ko inda take oum bata kallaba kai tsaye ta fita a palon hankalinta tashe tana sake kiran AK. Zaume takai raɓas akan sofa wani gumin tashin hankali na keto mata ina Ak yakai mata yarinyar mutane kana me rigar mace take yi a cikin part ɗinsa? . Waɗan nan tambayoyin sune cunkushe a ran oum jesrah kam har idanunta sun cika da ruwan hawaye. Maganar umaymah ta jiyo matar da setafi shekara bata ga ko wulginta bane a ɓangarenta amma sai gata cikin tashin hankali tana faɗar wasu maganganu marasa kan gado akan oum ɗin da AK "Wllh baze ketama ƴata haddintaba kuma kija bakinki kiyi shiru maryam! Bacin ya gama cin mutumcinta shine seya gudu da ita kenan duk lalatarsu da suka saba yi a waje be ishesuba saisun shigo harna cikin gida. Wllh maryam kin haifa mana balai da masifa a gida haba ace ƴaƴa sun gagari uban kowa tsabar su nunama mutane suɗin tantiraine jinin wulaƙantacciyar ƙasar nigeria ne ke yawo a jikinsu. To wllh sunyi kaɗan duk inda shegen yaronki yake ya fitomin da ƴata" "Kodai shegiyar ƴarkiba karki sake kuskuren shegantamin tsarkakkun yarana umaymah!". Oum ta faɗi a mugun hasale tana miƙewa tsaye. "Ki fice kibar shahi umaymah tun kafin ki tara mana ƴan kallo" ta sake faɗi tana mata nuni da kofar fita. Jesrah kuka take sosae na ganin tashin hankalin dake faruwa tsakanin iyayen nasu. Ficewa umaymah tayi tana saka ƙiran mijinta a waya. *BY AMMEY LAYLERH* A gimtse kawai. *🦅 MIKIYA 🦅* _A wonderful world & Special anti terroRism squad_ ____________________ *MARYAM NASEER MIRRAH* ~AMMEY LAYLERH ✍️~ ✯ *~🌠 JAJIRTATTU WRITER'S ASS.... 💫~* BOOK Two…………………………񆬍✍ 25&26 # HOT LOVE # ROMANCE SCENE # DESTINED # LIFE # REVENGE # AK MEERAH # IDENTICAL TWINS ★★ ★★ Yau kwananmu uku kenan a wannan gidan wanda naima laƙabi da baƙin gida, don kuwa tunda na shige shi ban sake sanya kafana ko ina ba daga ɗakin se bathroom iyaka rayuwar da nake yi kenan a gidan. Haka shima kullum baya fita ko ina muna a tare ne muna jinyar jikinmu, koma dai nace muke jinyar nawa jikin donshi tini ya ware ko wannan uban zafin kan ba ze hanashi bayyana rauninsa na jinyar da yake ba. Don shi mutum ne da yake iya shanye ko wanne irin abu ne don kawai karya bayyana rauninsa. Kulawa kamm iyaka kulawa ina samu sosai fiye da duk yadda me karatu zeyi hasashe, haka tun daga ranan be sake koda kwatan kwacin sake nema na bane. Amma fa kullum yana naniƙe dani ga wannan dattijuwar kullum seta shigo ta gasani tamkar wata me jego shi kuma yana aikinsa na bani magangunan disashe zafin wurin. Ban tabbatar da cewa hakan gata suke min ba seda cikin kwana biyu wannan mugun ciwo dama raunin da nayi ya disashe a cikin kwanaki biyu kacal. Duk wani rashin kirkina dama na daɗe da ajje shi a gefe tun daga ranar danaji shigar waɗan nan maganganun nasu moh da kuma umaymah, tun daga loƙacin tausayinsa ya sama matsugunni a cikin zuciyana bayan na gama fahimtar ko wanene shi, da kaɗan daga cikin labarinsu da jesrah ta guntsiramim. Banji inajin haushin abinda yamin ba sema ji danay da zan temaki mijina bakin rai bakin fama. Kuma ban bashi lefin komai ba tunda nida kaina nice shedar bayin kansa bane kuma baya a cikin hayyacinsa a loƙaci. Kuma Allah seya tseratar dashi daga sharrin zina tunda baya da haƙƙin kowa a kansa kuma ya kasance bawa me tsananin biyayya a gareshi . Tsaye nake na kasa fitowa daga cikin bathroom ɗin na kasa fitowa saboda nasan yana zaune a ɗakin kamar kullum gashi towel ɗin duk se ƙananu kuma babu bathrobe banan yadda akai suka fita a bayin ba. Chakk na tsaya nama rasa yacce zanyi da kaina gashi banson maida kayan dana rigada na cire kasancewar dama duk bana kirki bane,wani towel ɗin dana gani ne na sake daukowa dana ga yana da ɗan girma na ɗaura sai naga shima ɗin iyakacinsa saman cinyata ya tsaya. Sai kawai wata dafara ta faɗo min na ɗaura ɗaya a ƙuguna na samu daya kuma na ɗaura a ƙirjina sannan na ɗauko wani na lulluɓe kaina zuwa kafaɗana dashi. A sace na buɗe ƙofar na ɗan leƙo ganinsa zaune gaban laptop yana aikinsa na gado ya sanya ni fitowa Saɗaf saɗaf. Kallo ɗaya ya jefa min yaɗauke yaci gaba da aikinsa shi sai abin nawa ma ya bashi dariya. Ganin yadda ta wani chuƙurkuɗe a cikin towel's. dama kuma shi duka ya kwashe bathrobe ɗin bayin. Ganin duka idan ta sanya zulum zulum take fitowa tana janshi ƙasa ta hade gaban kuma ta tattare. "Kin makaro ma yarinya tunda so kike na tankaki wannan ɗin ai neman maganane!, ko dan kinga ban sake yunƙurin miki komai bane shi yasa kike yadda kikeso ohon miki" Zaram ya miƙe yana fatali da systerm nashi banyi aune ba se ganin mutum nayi zan gan gan gabana. Sena tayi wata ƴar filik dani,don nifa maganar gaskiya wannan uban tsayi nashi shi kaɗai firgitani yake kai wllh duk inda nake haɗa kiyastin tsayinsa da _PRABHAS_ wllh se nake ga kamar yama fi hakan. Duka tun daga sama har ƙasa yake bina da wannnan shegen kallon dana kasa iya jureshi har zuw yanxun kuwa, Se kawai na fara ja baya da baya shi kuma yana sake matsoni haka har nakai ƙarshen ginin. Cahkkk na tsaye ina ɗauke numfashi ganin se ƙara kusanto kans gareni yake. Hannunsa ɗaya ya sanya ya dafe jikin ginin ɗayan kuma na cikin aljihun wandon Three quiter ɗin dake jikinsa, ƙamshinsa kuma na cika min hanci yana toshe min duk wasu ƙofofi na shan iska, "Wai miye haka don Allah ka matsa shiryawa zanyi fa!" Na faɗi ina wani turo baki gaba idanunsa ya lumshe Yana buɗesu akan mitsil ɗin lips nawa dani kai tsaye bansan hakan illata zaman lafiyarsa yake ba. Banyi aune ba naji ya ƙarasa hade sauran tazarar dake tsakaninmu ƙirjinmu ya manne yana Jin kaman zai yaga duka abinda yake jikina yayi Watsi dasu. Harshensa ya ɗora akan lips ɗin nawa babu tsammani naji yayi musu lasan data Saka tsikar jikina gabaki ɗayanta tashi a take, Idanuwana na ciro na kallesa baki na na buɗe da nufin masa magana ya rufe bakin da Saka harshensa cikin bakin ya laso duka salive dake cikin bakina yana sake zagayoni da hannunsa. yana sake mannoni jikinsa da ƙarfi muka sake wata irin haɗuwan data sakamu sauƙe numfashi me sauti a tare yana sake zira harshensa cikin bakina cikin sanyi da wani irin mayen salo ya sake laso cikin tsakiyan bakina yana lunshe ido cikin wata irin yanayi me wuyan fassara. Ƙafafuntane suka soma rawa suna son gaza ɗaukana jikina na ƙyermar tsoro wani kalan nannauyan numfashin ta sauƙe daya Sanyashi buɗe jajayen idanuwansa sakamakon wata fitinanniyar tsotsan da yayima gefen lips ɗinta.Wuyanta yakai hannunsa ɗaya yana shafawa kafin ya mayar da bakinsa akan tsinin hancinta ahankali ya fara lasansa hannuwansa na gangarowa cikin rifin towel ɗin data chukuwkuye a cijinsa. Fisge towel ɗin yayi yana jifa dashi Akan shafaffen cikinta tafin hannunsa ya sauƙa daga shi har ita a tare suka sauƙe ajiyan zuciya. Cikin ya sake shafa tareda buɗe idanuwansa da kyar ya Kalli fuskanta datake haɗe da tasa idanuwanta a rufe tana kasa buɗesu saboda tsananin tsoron abinda yake matan. Tsakiyan ƙirjinta ya kalla daidai lokacinda yake zira hannunsa ɗaya zuwa kan ƙirjin ɗayan kuma zuwa tsakiyan bayanta cikin sanyi da wani irin feelings masu ƙarfin gaske. A tsorace ta soma ƙoƙarin kwace jikinta a nashi jin abubuwan da yake mata na neman yafi karfin ɗan ƙaramin hankalinta. Sake riƙota yayi yana me sake cusa hancinsa ya haɗe da nata yana gogawa cikin sanyi da mutuwan jiki, Jajayen idanuwansa da suke sake shigewa ciki tsaban wutar abinda ke neman zauta tunaninsa. Sauƙan ɗumin bakinsa da harshensa akan tsakiyan kirjinta daya raba da nata ƙirjinta . Wani kalan ƙanƙamesa tayi tana neman janyewa da sauri Amma bai bata daman hakan ta hanyar sake mannota ƙirjinsa da ƙarfi yana sake jefa bakinsa yana sake haɗewa da bakinta tsotsan bakinta yakeyi cikin salon da kanta ya kasa ɗauka yana yiwa cikinta zuwa kirjinta wata irin shafan dake sake sakata ruɗewa cike da masifan tsoron abinda take gudun ya faru. Ɗaukanta yayi cilak yana zama kan sofa tare da wani kalan lasan fatar wuyanta da harshensa, tsikan jikinsa suna tashi gaba ɗayansu hakama nata jikin wata kalan rawan tsoro yafara sedai be ma san hakan na faruwa ba. kan ƙirjinta ya gangaro da harshensa ya lashi fatar kirjin tareda lumshe idanuwansa dake neman juyewa. Kwacewa taso yi jikinta na ɗan rawa sedai motsawarta ya bawa jikinsu daman sake haɗuwa da kyau. Take control ɗinsa ya konce yana me ɗagata gaba ɗayanta ya nufi bedroom da ita har loƙacin bakinsa na cikin nata dukkanin jikinsu su biyun rawa yakeyi. shi na wutar abinda ke sake rura wutar abinda ke sake kunnosa zuwa son kasantuwa da ita. Ita Kuma na tsaban masifan tsorone da firgicin yanda yake tafiyar da ita mustu mutsun da take ne yake sake kashesa yana tayar da zaman lafiyansa. A kan ƙayataccen round gadon ɗakin ya kwantar da ita jikinsa har rawa yake. Ina ganin hakan wani mugun tsoronsa ya ɗirar min loƙaci guda. A tsorace na miƙe ina sake chukuychuye guntun towel ɗin da shi kaɗai ya saura a jikina, inda rigan da zan saka na nufa numfashina na fita da kyar da kuma tsoro. Rigar na ɗauka zan saka kenan na sake jin soft hannuwansa saman jikina haɓarsa ya ɗora kan dokin wuyana yana min wasa da jiki cikin wata narkakkiyar murya ya furta. "Me zakiyi da sleeping wear ɗin?" Cikin muryan kuka nace "Sakawa zanyi in kwantama bacci nake ji" "You don't need to wear anything to night" Nan take hawaye ya sake ɓalle min idona na zubda ƙolla nace, "Ni bazan iya kwanciya babu kaya ba a jikina!" na faɗi ina son zame kaina daga gareshi. Sake cusa kansa cikin wuyana yayi da wata matacciyar muryansan ya sake furta. ". Don't worry. I will cover your with my body" ya faɗi yana ƙarayin sama dani xuwa kan bedroom nashi. kuka na sakar masa domin tuna irin baƙar azabar da nasha daren shekaranjiya. Sosai nake sheshsheƙar kuka nasan yau kam idan yace irin abin ranar zaiyi min mutuwa ma kawai zanyi nasan na shiga, I have no way out no escape. Amma ni ban shirya ba tsoro nakeji gashi babu alamar sassauci a fuskarsa. Domin Abinda nake karantawa a idonsa shine yake ƙara bani tsoro,Idonsa ya janye daga cikin nawa. Cikin wannan sound nashi ya furta "Kuka kuma? tun yanzun? Me kikema kukan wai?, I did not even kiss you fa" Ya faɗi yana sake shigar dani cikin jikinsa tare da sake kissing na forahead nawa. Still cikin wannan muryan ya sake furta " Amswer mee mi kike ma kuka?". Cikin muryan na furta "Tso ro tsoro inaji!' Saman fuskana ya shafa tare da gangaro da hannunsa zuwa saman ƙirkijina,"Tsoron me kuma?" ya furta yana sakar min numfashinsa me ɗumi wanda ya sanya tsigar jikina zubawa. Da hannu na nuna shi, sake matseni a jikinsa yayi cikin gajiyayyar muryarsa ya furta "i promise 2 u i will never do like at the last time that fist day" wani kukan na sake saki A gajiye ya sake furta "Me kike so kuma?" Cikin cracking voice na furta ni dai ka ƙyaleni kawai!" Wani lalataccen murmushin gefen baki ya saki tare da faɗin. "IMPOSSIBLE" Kawai ina jin sauƙar lips nashi kan nawa lips ɗin very lightlyya fara kissing nawa out. Daga nan komai ya ɗauki seti tun ina iya roƙon ya ƙyaleni daga karshe dai harna hakura ina saddarƙawa, don kwarai na daɗe da fahimtar mutumin nan abinda yasa gabansa kawai yake yi, kamar kuwa yadda ya faɗamin ɗin lallai na yarda idan yace zaiyin to kuwa tabbas zaiyi idan kuma yace bazaiyi na yarda babu abinda ya isa sanya shi yayi ɗin koda kuwa menene shi. Zafin da naji bekai na ranar ba amma fa na jigatu ba laifi don ba karya na azabtu iya azabtuwa. Kaina na saman ƙirjinsa yana shafa sumar kaina a hankali ahankali tamkar wata baby lol. Se bayan shuɗewar wasu awanni kana ya ɗaukeni chilak yana yin cikin bathroom dani, wanka ya mana a tare kana ya zira bathrobe tare da shigar dani ta cikin nashin ya zaman munyi amfanine da ɗaya. Hannuwansa na yawo a wasu sassa na jikina haka muka fito a gefen bed ya zaunar dani yana sakin rigar wankan dake jikinsa. Saurin chukuykuye duvet nayi ina sauƙe ijiyar zuciya don wllh naga alamun mutumin nan bayda kunya ko kaɗan, ɗauke kansa yayi tamkar besan abinda ya aikata ba a nutsensa ya sanya wasu fitnead rober na bacci irin masu laushin nan farare. Iyaka guntun wandon kawai ya saki yana kwanciya gefena tare da juyo dani muna fuskantar juna, idona a kulle cikin sauƙe numfashin tsoro na ce " zan sa ka kayana" "Ba buƙatar hakan" naji wannan bugaggiyar muryan nashi ya bugi dodon kunnuwana. Rigima na sakar masa sosae ina dukan ƙirjinsa da babu riga wanda kai tsaye hakan ashe sake kunnoshi nayi, Haba loƙacin da naji yana sake ɗorani akan wata sabuwar hanyar tuni ɗan ƙaramin kukana ya koma na gaske wanda Allah ne ya temakamin ya kyaleni da ƙyar. ★ Acan masarauta kuwa sosae Alhussein ya nemi daya tada ɗan ƙaramin yaƙi dalilin rashin ganin Ƴar gaban goshinsa dolly. Ga kuma rigarta a ɗakin AK an gani duk wani sassa na ɓangaren sun gama cashe shi tsaff sedai babu kowa wasu wuraren kuma basu isa shigar saba saboda wani gun securityne wani wurin kuma da wani sassa na jikinsa yake amfani wajen buɗeta. Oum kuwa tana can a gefe abinta taja bakinta tayi shiru tama rasa wanne kalan tunani ne zatayi akan hakan, tasan dai har abada Ak baze taɓa kusantar zina ba duk da baka isa ja da ƙaddarar ubangiji ba amma tana da yaƙinin Insha Allah babu jininta babu aikata zina. Rashin ganin meerah dadai kam ta damu amma da zuciyarta ta hasko mata wani abu data haɗa da lissafin yasmine da kuma meerah ɗin duk kusan loƙaci ɗaya hakan ya faru se taji nutsuwa na zuwar mata kuma a take zuciyarta a haska mata wani abu. rashin samun AK a waya dama shi yafi komai ɗaga mata hankali har yanzu ma kuwa da wayan ke gabanta still tana trying na no nashi. Wasu ƙwararrun masana na'ura Da'da ya ƙira a wayewar cikar kwanaki uku, haka suka zo sashen Ak suka shishshiga binciken ɗakin da yasmine take. Anan palon suka ganota da ƙyar sedai duk yadda zasuyi su fiddo da dolly hakan ya gagara sosae hakan ya sake ɗaga hankalin su umaymah. Moh jiddoh kuwa duk wani tujara nata akan Oum take saukeshi tace dama jininta masiface a garesu, Ana haka kuma a daren ranar jirginsu Sarki Ash ya sauƙa a cikin masarautar. Ba a sanar dasu abinda ke faruwa ba an barsu se xuwa washe garin ranan sannan sun tsirga. Sedai hakan bata samu ba don moh tana jin labarin sun dawo taje har part ɗin da suka sauƙa su dukansu taje ta sauƙe musu wata sabuwar tijarar. sam hankalinsu be tashi ba kamar yadda taso ta haɗa rikici tsakanin iyayen yarinyar da kuma oum. Fitowar Anne kenan daga bathroom bayan ta watso ruwa taji irin tijarar da moh take saukewa iyayenta wanda yanzu a duniya gani take bata da sama dasu har gaban abada tunda har Allah ya bayyana mata su. Chakkk maganar nata ya maƙale sakamakon ido biyu da sukay da Anne dake binta da wani kalan matsiyacin kallo, don kallo ɗaya tama matar taji sam bada mata ba, Kowa inda Moh ɗin take kallo kamar idonta ya faɗo kasa yabi da kallon don ganin abinda yake neman ruɗar da ita. Wani kalan tattausan murmushi queen lajja ta saki tana me sake zamanta na crossing ƙafafunta datai. "Miye abin firgicewa kuma jiddoh? Bafa *JADDER'N ASHAAN* Bace wannan ɗin EASHERH ASH Ceeee ɓatacciyar ijiyar Allah" (KAI WLLH SENA TSEYA INA CIKIN RUBUTUN NAN KEWAR MY TEAY NA TA FAƊO MIN I MISS U MY TEAY ƊIN MIIIRAH I WILL MISS U MY TEEMERH NAAAAA! MY TEEMERH'N MERRY) {HHHHHHH seni masu sunaye da yawa😀😁😂😊} Wani kalan tsuma naman jikin moh ya fara wata zufa na karyako mata tana biyowa ta duuka sassan jikinta. Ja da baya da baya ta fara yi idanunta na fara gani bibbiyu numfashinta kuma na gwamewa. Karo taji tayi da wani abin da batasan ko miye ba saurin dafe goshinta tayi tana ciro kanta don ganin da me ne taci karo haka?. Wani kalan dafe kirjinta tayi tare da zaro idanuwanta waje don ganin wacce bata taɓa zata ko tsammanin ganin bace tsaye agabanta. Baki ta buɗe da niyar sakin ihu sai kawai ta tafi luuuuuu tana zubewa some a wurin..... _Hhhhhhhhhhhhhh ko me ne ya firgitar da moh haka?_ _Tofa mike shirin faruwa ne da meerah ɗinmu uyummmmm?_ _Tofa queen lajjanmu irin wannan yaɓa magana haka? Amma ba komai nidai ina yinki tare da my teay Naaaaaa ma itama tace tanayinki for ever_Ga My kilan ɗina ma tace tana yinki itama ma my piepie'n Mirrah_ Amma ita My Meji love tawa itace tace wai YAYA KUWAIT AK take yi😆😆😆😆 _ _Maman mujaheed da Aysha kuma tace ita ta Meerah ce_ My zeey musa ma ta ɓangaren meerah ce_ Amma ai duk babu ɗamuwa ma tunda mun zama ɗaya da Yaya kuwait Ak ɗin nima na ɗana lol😁😂_ _Allah sarki my Ummeerh musa kekam banma san mine zan ce miki ba keda Hassana Yahuza ƙaunarku ta musammance gareni, ku duka kuka haɗa kuke sonmu DA Yaya kuwait AK ɗin da my Meerah ɗin ba. Ban manta da tarin kaunar da kuka nuna min a duka sauran littattafaina ba kunso JALAAL AREEF kamar ba gobe haka ma MALEEK TOUFIQ, Haka ma ALIEYO namu na gargajiya mutumin Hajjo ɗinmu ta gargajiya hhhhhhh lol itama 😂😁 wllh ta bani ciwon kai ba laifi..... Laaaaaa nifa na manta irin zazzaga wannan jawabai haka *END😱* Amma fa bana littafin fa na fage ɗin don se yanzune ma hhhhhhhhh *🦅 MIKIYA 🦅* _A wonderful world & Special anti terroRism squad_ ____________________ *MARYAM NASEER MIRRAH* ~AMMEY LAYLERH ✍️~ ✯ *~🌠 JAJIRTATTU WRITER'S ASS.... 💫~* BOOK Two…………………………񆬍✍ 27&28 *Bɪꜱᴍɪʟʟᴀʜɪʀ Rᴀʜᴍᴀɴɪʀ Rᴀʜɪᴍ* ♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡ ★ Kowa na ɗakin da kallon rashin sani yabi matar dake tsaye wacce suka tabbata ganinta shine yay sanadiyayyar sumewar moh, amma banda queen lajja data ƙame a zaune tana rasa ma wai shin a cikin wacce duniyace take ma takamaimai. Jaddernta dai? Aminiyar nan tata dai wannan ƴar uwartata ƙanwarta jininta biyuninta dai wacce ta riga da fidda rai da sake ganinta har gaban abada wacce ta mace a garin haihuwarta ta farko a masarautar EMAAR's wacce aka nemi gawarta sama ko ƙasa aka nema aka rasa se iyaka yaronta suka gani shima a ma ce. Shi yasa a loƙacin da sarki Al-hussein Ashaan yazo da batun nemawa ɗansa Hassan Al-hassan auren ƴarta RAZEENERH (Mah) taki ta rufe ido tace samm bata yarda ba. Wanda seda aka kai ruwa rana kana ta amince bisa tilastawar mijinta sarki Ash yace ai ba'a taɓa gudun ƙaddara duk inda kake idan zanen kace seta bika ta zana haka don haka ma kar ɓacewar ƴar uwarta ya nemi da juya mata brain nata. Ita kaɗai ta rufe tayi tayi kuka tayi kuka a loƙacin da auren ƴarta Raneenerh ya ɗauri da Hassan Al-hassan EMAAR's don gani take itama tana iya mutuwar a rasa nata gawar sedai hakan be faru da ƴar tan ba seya faru dai da ɗayar ƴarta wacce a masarautar suke ma kallon ƴar asalin EMAAR's ce. ɓacewar Eaherh Ash a EMEER's shine mabuɗin komai don anan hasashen kowa ya koma kan cewa lallai Jaddern Ashaan ba mutuwa tayi ba ita ma batar da itan akai. Wannan kenan. Jikinta har rawa yake wajen rarrafawa ga ƴar uwar nata biyuninta kuma babbar aminiyarta jaddernta *JADDER'N ASHAAN* Dinta mace mafi soyuwa a zuciyar mijinta ASHAAN. Wacce akayi bikinsu rana daya aka kaisu ɗakin aurensu rana ɗaya wacce seda tama biyuninta rakiya har ƙasar kuwait masarautar Emaars kana itama aka mikata ga nata mijin sarki ash wanda suka kasance suɗin aminan juna ne. Su kuma sun kasance ƴaƴana ga babban limamin masallacin kaab dake garin maka wato *SHEIKH ALIYULLAH DAWOOD* Itama jaddern ɗurƙushe takai ƙafafunta ƙasan tana meyin sujjadr sukr, da jan kafa kowa ya isa ga kowa suna wani kalan ƙanƙame junansu kuka da dariya na kwace musu a loƙaci guda. Ɗago kanta queen lajja tayi tana sake duban biyunin tata sai kuma ta sake fashewa da kuka tana sake ƙankameta cikin muryan kuka ta shiga faɗin. "ALHMADULILLAH! ALHMADULILLAH lallai godiya ta tabbata ga Ubangijin da ke bayar da kyauta ga bayinsa ba tare da duba cancanta ko matsayin su ba a duk sadda yaso, godiya ga Ubangijin da ke ruɓanya ƙofofin rahamarsa ga bayinsa, godiya ga Ubangijin da ke wanzar da farinciki ga zuciyar kowacce halittar rai me numfashi, godiya ga Ubangijin da ke fidda matacce a cikin rayayye,godiya ga ubangijin dake raya rayayye a cikin matacce! haƙiƙa cikekkiyar godiya ta tabbatane ga sarkin da babu kamarsa sarki buwayi gagara misali. Sarkin dake juya dukkan al'amuransa a sa'ilin da yaso. Shukar nan dai da ba'aso ta ruɓanya ba ubangiji yayi alƙawarin seta ruɓanya koda ko ba daga naki tsatson bane Allah yayi alƙawarin se jinin Sheik Aliyullah dawood yayi rayuwa a masarautar nan kodan dattin zunufin da aka jima ana aikata da ruwa me tsarki tsarkakken ruwa" Queen lajja ta faɗi tana me sake kai goshinta ƙasa. "Bare ma harda naki jinin cikin wanda suka ruɓanya sukay yabanya a cikin Ashaan mention! Gana nan HASSAN AL-HASSAN ASHAAN shiɗin gudan jininane seda ya huɗa cikin jikina kana ya faɗo duniyar, daɗi da ƙari harda ma harda tukwicin tsarkakkun ƴaƴa dama jikoki" Chakk ta tsaya sakamon sanyin idaniyarta wato AK daya sarƙafo hannuwansa cikin nata cikin wani kalan mur da face ya furta "Pls duk wannan ba yanxun ma HASKE'n EMAAR's" gashin kansa ta shafa tana me leƙa bayansa Meerah dake ta wani ɓoyewa a bayansa ta kamo nata hannun tana jimƙewa dana AK da natan wasu hawaye masu zafi da sanyi na zubo mata. "A cikin wannan duniyar har gaban abada kune hasken haske! Kune haske maganin ko wanne kalan duhu, ubangiji ya sanya ma aurenku albarka ya ruɓanya muku da zuriya ta gari nasan a yanzun banda matsala dakai tunda ita ɗin zabin kac...... Da sauri AK Ya toshe mata baki yana wani muzurai yana rarraba ido shi a dole ba zata kunyatashi gaban mutane ba, tattausan murmushi ta saki nasu na manya da sauri queen lajja da se yau take ganin meerah ta janyota tana rungumata sosae "AUTAR AHLI" queen lajja ta faɗi tana sake jin ƙaunar ƴar uwarta da ƴaƴanta biyu da ubangiji ya bayyana mata su duka a loƙaci guda duk wannan abinda dake faruwa sarki ash be sani ba haka ma sarki hassan wanda yana daga can inda yake daidai da shigowarsu AK tare da JADDER'N ASHAAN cikin masarautar yaji zuciyarsa ta wani irin bugawa tare da motsa may da karfin da seta ya tashi zaune daram. "AH!MINHR!" ya faɗi yanajin zuciyarsa na sake motsawa sosae akan muradi da kuma ɗokin ganin Mahaifiyar da sedai ya ganta ta cikin woya. Mahaifiyar da besan daɗin taba, mahaifiyar da aka rabashi da ita ba tare dako numfashinta tare da ɗumin jiki irin na ɗa uwarsa an barshi yaji ba. Jinsa yay ƙaƙare yake da son ganinta amma kuma komai ze tafine yadda aka tsara ɗin, don haka ya danne duk wani shauƙi da son ganin *AH!MINHR* ɗin nashi zuwa wayewar gari. Kishin giɗen da yake ya koma yana dafe setin heart nashi don jin yadda take may taka da luguɗe harda lillisa. ★ Queen lajja ce ta mike tsamm tana nufar gaban deep frigde ɗin ploor'n, ruwa me sanyi ta ɗauka tana yayyafama Moh wani dogon numfashi ta kawo tana tashi a zabure. "Ina!!!? Wllh hakan bame faruwa bane har gaban abada, nariga na gama da wannan babin koda ace JADDER'N ASHAAN ce tsaye a gabana dole zata kasance cikin hali na hauka bare ma nasan hakan bame iyuya bane! Haba ni wllh se ma yanzu na tuna ashe fa mafarki nake Hmmmm" taja ijiyar zuciya tana me sake faɗin "Kaidai wannan yaro uwarka ASIA da ubanka ASAAD basu iya haihuwa ba se kuma ta shiga lalabumen neman Inda jaddern ashaan ɗin take don itafa tun waccen ranar se yanzu ne komai yake dawo mata na inda ta tafi wurin jaddern ashaan ɗin mahboob kuma yabita, to tana faɗuwar nan yasauri ya soka mata allurar mantau ta tsahon wani loƙaci kawai data buɗi ido ta ganta ba zata iya tuna kome ya faru ba. Shine dalilin da bata ko sake tunawa da taje ɗaukar jaddern ashaan ɗin ba se yanxun. Wanda kai tsaye hakan umarnin mahaifinsa ne ASAAD EMAAR's wannan shine tafiyar waccen ranan da muka shallake kenan. Jindai har yanzun hannunta be kai inda take saka ran bane ya sanyata buɗe idanunta. Tarrr kuwa se akan jadern ashaan da zuwa loƙacin take zaune kan wata cuisine sofa fara. Sake mitsitstsike idonta tayi tayi don ganin kamar ba daidai yake bata ba. "Ganinki rass yake Jiddoh! Baki sami raunin gani ba tabbas ni *EASHERH SHEIKH ALIYULLAH DAWOOD* {JADDER'N ASHAAN} ce zaune gabanki cikin rai da kuma ƙoshin lafiya, da buƙatar yanzun kam kije ki huta don nima barci nake ji" Jadderh tayi maganar tana me kallon AK. Shima inda meerah take ya kalla sake shigewa jikin lajja tayi, ita kuwa cike da irin abin nan na jika da kaka ta turota tana faɗin "uhummm nan kike woni maƙale min ina nan kika bi mijin naki kuka guda kika bi kika ɗaga ma baiwar Allah hankalinta" sake lafewa jikin queen lajja'n tayi tare da turo bakinta gaba "To ai naga saceni yayi kunsan jikan naku ya ƙware wajen kizmashin mutane" tayi magananta kai tsaye tana sake ƙanƙame hannun lajja don wllh ta rigada ta rantse ita da mutumin nan se gani se hange se gani daga nesa kuwa. Jadderh ce ta kamo hannunta ana lajja tana zaunar da ita daga gefenta tana me faɗin. "Ni taho wurina kyale anush laj tare dake zan kwana ni ɗiyata don bazanyi wasar jika dake ba" Da ido kawai Anne kebin waɗan da suka zamo a yanzun sune halinta. Ganin yadda suke nunama ƙaunarta ƙauna wato Meerah. Ita kuwa a duniya me zace da waɗan nan mutane bayan taci gaba dabinsu da adda'oin tsari daga mahaliccinta. Uban ihun da moh ta saki ne ya dawo da hankalin kowa kanta ko kafin tayi wani yunƙuri ASAAD da shigowarsa kenan ya danna mata allura a gefen wuyanta yana tare ta faɗa jikinsa some. Kai tsaye woje yayi a bakin wata rantsatstsiyar car ya tsaye kwantar da Moh yayi yana reverse tare da barim harabar wurin baki ɗaya yana me nufar nata sassan. Be sake bi ta kansu ba ya fice a room ɗin baki ɗaya, anan jadder'n Ashaan ta kwana tare da Meerah.Kai tsaye katafaren Apertmen nashi ya nufa seda ya sakarma kansha shower kana yayi adda'ar bacci yana kwantawa a lafiyayyen gadonsa daya gaji da haɗuwa, cikin tattausan farin duvet ya naɗe wanda keta tashin wani kalan mayataccen unique ƙamshinsan nan da baya taɓa barin ɗakin. A Hankali ya shiga buɗe lumsassun idanunsa dake rufe cikin mayen bacci. sakamakon mummunan mafarkin da yayi cikin abinda bai wuce mintuna 50 ba. A hankali gumi ke saƙƙo masa yana wanke shi daga shi har sleeveless singlet dake jikinsa,water bottle dake saman couch ya fara buɗewa ya tsiyaya a cup dake gefen bed ɗin kaɗan ya sha, wani kalan fusgar da iska yayi yana sake jan wahalallen numfashi da ajiyewa kafin ya fara motsa bakinsa slowly yana me furta. "A'uzhubikalimatillahit'tamaat min sharri maa khalakh. Laa ilaha illa anta's subhanaka inniiy kuntu minaz'zalumiiyn!, Laa ilaaha illallaahul'azheemul'haleem,laa ilaaha illallaahu rabbul'arshil-azheem,laa ilaaha illallaahu rabbus-samaawaati,wa-rabbul-ardhi,wa-rabbul-arshil-kareem" ya faɗi yana me dafe setin saman goshinsa. Ya ɗauki tsayin loƙaci yana maimaitawa duk wata aadda'a da tazo bakinsa kafin a hankali ya lumshe idanunsa ya buɗe yana ɗan jansu luuuuuu ba da yawa ba, gefen lips nashi ya ɗan cija da haƙoransa. Shi kansa bazaice ga kimanin loƙacin mai tsayi daya ɗauka a zaunen ba then kamar wanda aka tursasa ya janye bedspread da ƙafafunsa ke ciki ya ajiye su cikin adjustable velcro slides slippers mai ɗauke da tambarin Puma kalar blue. gefen bed ɗin ya dafa da duka hannayensa slowly ya koma yana sake zama yana lumshe kyawawan idanunsa na tsayin loƙaci, Tun daya shige bathroom ɗin yake tsaye ƙarƙashin shower hannayensa dafe da jikin wall guda na katafaren bathroom ɗin da yaji kayan mo re rayuwa. sake sunkuyar da kansa ƙasa deeply thinking about his dream, A ƙalla ya ɗauki loƙacin da bai san adadi ba a ƙasan shower ruwa yana ci gaba da dukan jiki da kuma kansa. Anan gefen bed nashi ya zaune jin yay har xuwa yanxu zuciyansa bata dedeta ba wani kalan wawan tsaki yaja yana tashi daga gefen bed ɗin da ya zauna ya nufi deep fridge,buɗe fridge ɗin yayi kwalaben Alcoholic wine dana whiskey, tequila,Vodka and orange juice ne sai container ice cube, kwalbar red wine ya ɗauka tare da cup sai ice cube daya zuba cikin bowl,komawa yayi ya zauna ba tare da ya rufe fridge ɗin ba buɗe kwalbar wine ɗin yayi ya zuba a cikin cup tare da ice cube, A Ƙasaitance ya fara ya shiga shan wine ɗin yana fitar da wani irin numfashi tas ya shanye ya sake zubawa sai da yasha 3 cups kafin ya ajiye yana fitar da wani irin huci mai zafi,idanunshi sun ƙaɗa jawur har wasu ruwa ruwa ke kwanciya a cikin su, cigarattes ya kuna yana fesar da hayaƙin sedai hakan be rage komai daga abinda yake na yankar zuciyarsa ba.bath ya koma tare da sake sakarma kansa ruwa har ruwan na shige may ta ido da baki. A sannu ya fito west nashi ɗaure da towel ɗin da yama woni kalan lago lagon ɗauri, gashin kansa na yararar da ruwa. Jiyay ma baki ɗaya zaman room ɗin ya isheshi ta babban ploor'n shi ya ratsa yana faɗawa cikin wani torture room ne ma za'a ƙiranshi nema ko kuma a ƙira shi da prison ko guardrooms. then midi wooden table da kujera da suke gefe and long cutains masu sauƙin haske da suka zagaye duka windows da entrance na room ɗin. "Ya Rahman!" ya furta a sadda yayi ganinsa ya sauƙa akan yasmine wacce ke kwance baje cikin deskaciom chiar. Da alamu rashin cin komai ne ya somar da ita kansa ya ɗauke a kallonta yana me tsallaketa wasu ɓoyayyun abubuwansamasu muhimmanci ya ɗiba yana sake tsallaketa. Wayansa ya ɗauka kai tsaye waya yayi ta kimanin minti biyu. Mahboob ne yashigo har room ɗin kai tsaye ɗakin da yasmine take ya nufa ɗaukarta yayi yana gyara mata bajewar gashin hatacimen nata. Tare da sake ja mata guntuwar rigarta ta ciki, ta ƙofar baya ya shigar da ita ya kwantar da ita akan sofa fridge ya buɗe ya ɗauki PEACH DRINK ɗin da shi kaɗaine a cikin fridge ɗin. Don mamallaka gidan sunyi son lemun fiye da sauran lemuka sei swan na almuera da suke amfani dashi so be samu ruwan ba don haka ya ɗauko Peach ɗin yana juye mata tun daga saman kanta har xuwa cikin jikinta. Duka tittikar abin lemu'n na maƙale mata a saman kai ai kuwa a firgice ta tashi tana kwala uban ihu se kuma ta fara yunƙurin mikewa tana neman hanyar guduwa. Tsintsiyar hannunta ya chafka tare da falla mata wani uban mari ai kuwa a take ta dawo cikin natsuwarta da taitayinta tana komawa dagwash akan sofa'r riƙe da kuncinta. Wani shegen worning ya buga mata yana fice a room ɗin tana ganin fitarshi da kamar mintina goma ta sake fasa wani uban ihun tana dirowa akan sofar ta fara birgima tana ihu, a guje sega mahaifiyarta nan ta faɗo ɗakin tare da wasu barori biyu da suka biyota, wata shegiyar tsawa ta buga musu tana fadin su ɓace mata anan. Sim sim suka fice kamo dolly'n tayi tana faɗin ta faɗa mata abinda ke faruwa amma se faman kuka take cikin muryan kukan take faɗin. "Mommah shike nan komai ya ƙarasa kwace mana da gaske ba zan taɓa samun saba! Kuma baraku taɓa ganin ƙarshen saba don wllh wannan mutumin da kuke kalla ba mutum bane kai a cikin aljannun ma se antona kafin a samo hatsabibi irinsa. Duk uban haɗarin kwayar nan haka ya jure mata wllh nidai yanzu tsoronsa nake ma mommah!" "Ai kuwa ni nan nayi alƙawarin ganin bayan ahlin maryam tare da Razeenerh kai harda ma waccen shegiyar Adeenerh'r duk sena ga bayansu da zuciyata zata iya samun kyakykyawar nutsuwa da salama" Umaymah ta faɗi tana huci tare da ajje kan dolly a ƙas tana ficewa a ɗakin.ita kuwa ci gaba da maganar ta tayi tana faɗin, "Wllh yau na gama yarda AK ba mutum bane kamar yadda sauran almumma suke faɗi! Don wannan ƙwayar idan na sawa mutum kusan haukacewa ma yake akan buƙatar kawai ya kusanci mace, idan kuwa be samu ba wllh mutum har haukacewa yake idan yazo ma da sauƙi ne ma mutum yake sumewa, amma shifa ko gezau beyi ba kana me yasa da naje gareshi memakon ya rarumeni cikin hauka da fita hayyaci seya kare da shaƙata ya cillani shegen baƙin ɗakin san can me kama da torture room ne ma za'a ƙiranshi nema ko kuma a ƙira shi da prison ko guardrooms koma fin haka don ni kaɗai nasan kalan azaban da nasha kafin na some....... Haka dai tayi ta maganganunta har wani shegen barci yayi awon gaba da ita anan kasan sofar. *A DAREN RANAN* Kuwa tunda ta Moh kwanta ta kasa ko runtsawa bare kwakwalwanta ya sama hutu yanda taga dare haka taga rana. Don tashin hankalin da take ciki allura kaɗai bata isa iya hanata runtsawa ba. Ganin komai take a baybay wayanta ta ɗauka ta ringa dokama Hussein ƙira amma wayan daya shiga se a katse. Ranta sosae ya ɓaci da abinda hussein ɗin ya mata na rashin ɗaga ƙiran da bay ba. Shi kuwa hussein a daidai wannan loƙacin yana a buge yake umaymah ta bugar dashi ta hanyar amfani da wasu ƙwayoyi masu ƙarfin gaske ta shayar dashi a cikin *PEACH DRINK* na fruit Tunda ya zauna a gurin ya yi wani irin shiru mai shiga zuciya be sake ƙoƙarin koda motsawa ba bare yayi tunanin yana raye? Ya suma? Ko kuwa mutuwa yayi? Duka dai ga gashi nan ne tamkar butum butumine. yanayin yadda yiyi she looks so restless and disturbed,wanda da kyakykyawan kallon tsanaki guda zai yi saurin sawa mutum ya fahimci yanayinsa yafi kama da na mutumin dake duniyar somewa. Shi yasa duk uban ƙiran da moh ta ringa doka mai woyan na gabanshi amma shi kansa shigar ƙiran ji da ganinsu yake ba'a cikin tashi duniyar komai ɗin ke faruwa ba. anan inda take zaune anan taga wayewar gari ko salla da aka shiga kasa koda motsawa tayi don gani take da tayi wani kwakwkwaran motsi komai na iya wargaje mata. Ƙarfe shidan safe na bugawa ta dokawa ƙungiyar baƙaƙen kaya ƙira kan su shigo EMAAR's Mention's anyi kisan kai da kuma kiddnapping yarinya. Ƙarfe shida da rabi sega jiniyar manyan baƙaƙen motocin ƴan ƙungiyar Human Right tare da SS da ƴan sidin difel sun cika bakin katon get na EMAAR's. Kowa besan abinda ke faruwa ba se ita moh ɗin kawai don haka ta ƙira security'n bakin get tace su barsu su shigo. Ta Apertment ɗin Hussien ta nufa da ya dawo daidai ɗinsa har yana ma shirin fita. da hannu kawai ta masa alamun ya biyota don so take yau ayita kawai ta ƙare yau kowa ma ya huta, don ta daɗe da tanajar komai da tasan zata yaƙesu. Kuma a yau take son ta girgiza zuciyar kowa har hakan yayi sanadiyyar bugawar zuciyar wasu zuciyoyin. Ta zama daga ita se ƴaƴan tane kawai zasu mulki EMAAR's EMIRATE's HOUSE. ★ Ƙarar jiniyar motocin da sukaji shine ya janyo hankalin kusan mafi rinjayen ƴan gidan, kowa ya fito a babbar mahaɗar duka sassan yake cin burki don ganin........... _To ai shikenan semu gimtse koooooo😀?_ Don Allah idan baki biya ba kada ki karanta min littafi, typing wuya,baya kamar ya ɓalle😢😬😟😰 don haka idan har kin shirya bin *AMMEY LAYLERH* da ɗarinki biyar domin ayi tafiyar manya dake Hajjajo🙅🙌. Kibar tagumi😱 nibance kowa yayi tagumi ba tsakaninki da Allah idan har kinsan halin ɗari biyar ɗinne baki da to nayi haƙuri ki turim ɗarinki Huɗu nikuwa na antayaki *PAID GROUP* namu da muke posting kullum Insha Allah..... *Idan kin shirya saya saiki min magana a wannan number'n* 08104493215 *Idan kuma kai tsaye account nawa kike da buƙatan shima ganan* 3206656358 Maryam Nasiru Fisrt Bank *Sayen na gari maida kuɗi gida koba haka ba😟😵😰 Don Allah karmu ɓatama juna loƙaci idan baki shirya sayaba karkimin magana, Masu zagina harda ma masu kiran ai ance marubuciyar MIKIYA ta rasu ku sani Allah ne me kashewa da rayawa. Wata ma data tambayeni nace mata paid ne kai tsaye cewa tayi shikenan tama samu* _Kunsan dana tambayeta inda ta samu me tace min? Kai tsaye cemin tai a wurin ƙawarta, ni kuma sai nace mata saidai kuma banma fara rubutun part Two ɗin so dan allah a faɗi alkhairi ko ayi shiru😯_ *🦅 MIKIYA 🦅* _A wonderful world & Special anti terroRism squad_ ____________________ *MARYAM NASEER MIRRAH* ~AMMEY LAYLERH ✍️~ ✯ *~🌠 JAJIRTATTU WRITER'S ASS.... 💫~* BOOK Two…………………………񆬍✍ 29&30 *Bɪꜱᴍɪʟʟᴀʜɪʀ Rᴀʜᴍᴀɴɪʀ Rᴀʜɪᴍ* *JUMA'ART MUBARAQ IN ADVANCE 🤝* ~SPECIAL TNX MY PEOPLE MASOYA MASU NUNA ƘAUNARKU GARENI AKODA YAUSHE👏🏻👏🏻🤛🏻~ DEDICATED TO UMMIE MUHD NASEER (Maman Humieratou) & AISHA AHMAD {Maman Hanan} & SALMA SUNUSI (Maman Nana) & HAUWA SABITU {Maman Junior}. Wannan fejin ƙyautarsa sukutum na baku mutanen amana nana. ♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡ ★ Daga yanda yake tsaye saman bene hannayensa harɗe yana kallar komai tub daga shigowar manyan motocin yana kuma nazartar komai, wani shegen murmushin gefen lips ya saki hannunsa ɗaya zube cikin aljihun wandonsa ɗayan kuma yana sipping zazzafan tea. Saƙƙowa yayi cikin taku irin na wanda jinin mulki da ƙasaita ke yawo a jini da kuma ɓargon jikinsa yake yake saƙƙowa cikin wata kalan zarra. Duk inda ya gitta se dogarai sun zube masa kai tsaye ya nufi room dasu lajja suke. Kowa da kowa yana tsaitsaye wasu hankalinsu tashe wasu kuma nabin baƙin fuskokin da suka ƙaru da kallo na ƙurillah. Zaune yakai saman kujerar alfarmar dake parlorn fuskarnan ɗinke kansa babu pcap ɗin gadon, blue trouser ne a jikinsa se wata shegiyar riga me walwali da ɗaukan ido, sammmm rigan bata da wani dogon hannu iyakanta saman shoulder nashi. Kanshi da nake da tabbacin a daren jiya yay masa wani kalan ɗan iskan aski tamkar an sanya yatsu uku ne an kwakwaye shi a wani karkace. Bayan shatin zanen da ya bada kamar na yatsu kuma akabi ta kan zanen aka rubuta *ÆK* wata daban ta ƙasan keyarsa kuma shima an zezaye babu wannan shilin gashin dake shan gyara. A wani irin salon tafiya da tunanin mutum aka rubuta *ÉÆGLĒ* shima kansa yanda aka rubuta eagle ɗin abin a kallane. Jesrah da fitowarta kenan tana ɗan missika idanunta cikin muryan bacci ta dubi AK tare da tambayar shi. . "Akiey wai me ke faruwa ne.? Why are you like this naga kowa da kowa ga jiniya ya cika gidan?" se ma yanxun idanunta ya sauƙa kan sauran mutanen dake zagaye da porlour'n. Idanunta ta sake missikewa tana sake sauƙe ganinta akan Anne da kuma mah seta kalli jaddern ashaan, idan ta kalla lajja seta dawo ta kalla jadderh se kuma ta kalla queen lajja tare da anne da suke kwasar wani mugu mugun kamanni na tashin hankali, A haka dai ita wllh ita se wancen matar take ɗibar yanayi da paah ɗinta ba idan har ba gizau idanunta ke mata ba. Sake kallon Ak tayi har jikinta na ɗan rawa "Akiey waime ke faruwane?" Ta sake tambayarshi a kiɗime da hannu ya mata nuni da *JADDER'N ASHAAN* "Hi is my grendpaah jes'r" taji muryansa kamar an kwasa mata tsawa a tsakar kanta. Da wasu irin idanu Jesrah ke duban yayan nata ba wai don ta gama aminta da kalaman da suka fita daga bakinsa ba, tuni barcin da take ji ya wartsake duk da ita ɗin journalist ce bayau suka saba ganin ɗaukar labarai makamantan haka ba amma taya za ai rana tsaka a ce wata ta daban itace grendpaa nasu? Ina ai abin hankali ma ya fita daban kumama tasan inda hakane ai da ko a labari taji kishin kishinɗin zance amma me ko a mafarki bata taɓa jin saɓanin hakan ba bare a gaske, hakan ya sanyata sake duban ak ɗin tare da faɗin. "Akiey ka kuwa san mi kace? Grendpaa kace min fa ita kuma jiddoh fa?" "Kwarai kuwa itace hasalin grendpaah naku! Kuma a ta dalilinta komai da yake kan faruwa suke faruwa. Wannan matar da take tsaye a gabanki ba kowa bace ita face muguwa azzaluma maciya amana, wacce ta aure min miji ta kuma shigo gidan taimin banka banka tai babakere. Tun daga loƙacin da margayi Sarki Ashaan ya aureta na dena gane masa a komai bana gabansa yadda kika san anyi min yaɓen jaɓa haka na koma a gareshi..... A komai Jadder'h itace gaba saboda ita His voice was clear and sweet as fruit from the vine. Though it wasn’t loud, it seemed to echo between the wife & wifey ni tamkar ba mata nake ba a gareshi. A kullum koda yaushe me martaba yana tare da ita daya samu intervals free haka yake ɓata loƙaci wajen ƙiranta a waya,su shafe tsayin loƙaci suna maƙale da juna,Sosai shaƙuwarsu take sake ƙaruwa soyayyarta na daɗa ke waye ko wanne longu da saƙo na sassan jikinsa. Kwatsam sega Jadder'h ta fara laulayin ciki babban ƙalubalen dana sake fuskanta kenan cikin wannan shegen yaron daga nan se sunanta ya tashi daga JADDERH, zuwa *JADDER'N ASHAAN* kowa da kowa na murna da farin cikin bayyanuwar cikin jaddern da kowa ya jima yana saka rai tun daga gareni amma se gashi rana tsaka wata tazo ta kwace matsayina da mijina dama komai nawa kowa ka kalla a wancan loƙacin zaka ganshi ne da wani irin maɗaukakin farin cikin da baka taɓa gani ba,kowa ka kalli fuskarsa da yanayin kulawar da yake bata ya isa ya tabbar da tsantsar ɗaukin da suke ga cikin nata,but still a time ne ɗin kuma wata sabuwar matsalar ta sake kunno min kai wato ya zamana ma ni zama photo a gareshi don a gabana zeyi ta ƙiranta video cool idan ba'a ɗakinta yake ba duk loƙacin da zai kirata ya ringa tambayarta lafiya kuwa? ko yaya yaga canji a tare da ita ya ringa tambayarta kenan ko tana lafiya? Idan ya tambayeta babu matsala wani bin tace abu kazanta yana mata ciwo wani bin kuma takan ce masa babu,every day within 12 hours they spend countless hours suna aikin abu guda,yanzun zai kirata after a few minutes he will just make a call again badon komai ba sai dan ya tabbatar da lafiyarta,video call kuwa yadda suka maida shi kamar cin abinci yafi musu wuya, duk kuwa da cewar muna a tare ne a cikin wannan masarautar dai. Hakan da yay min ne yasa naci alwashi ramawa akan ita abar son nashi daya fifita akaina, wannan shine silar da yasanya komai yake faruwa na reni Hassan tun daga wannan ranan amma koda da sau ɗaya ban ɗaba jin soyayyarsa. Na rayu ne da tunanin idan ya girma na wulaƙantashi. Hukuncin kakarku shine kuma ya biyo ta kanku na ɓatar da babbar ƴar Hassan wanda ni naɗauka itajin jininsace. Ashe ba haka bane tshohon munafurcin uwarsa Jadderh ya kowa ta hanyar ɓoyemin gaskiyar lamari, nice nan nai sanadin barin Yasmine daga cikin wannan duniyar, (UWAR ADEENERNERH) wacca bayan mutuwar tane sarkin kano ya sake bama Hassan auren ƴarsa Wato jinin mayu (MARYAM) kenan mahaifiyarsu AK da ZAID. ni ce na kasheta da hannuwana kamar yadda na kashe kakanku ni kuma mijina da hannuwana, bana bama kowa aiki nidai karin kaina nake aiwatar da nufi na akan mutum ba tare da samun saɓani ba. Sai dai Ashe nima loƙacin ina ɗauke da nawa cikin ban sani ba..... "ki ka gyara a wasu zan tukan naki moh cikin tsohon bafaden abaa dai.... Suka jiyo muryar *ME MARTABA SARKI HASSAN AL-HASSAN ASHAAN* wanda yake tsaye daga bakin ƙofar shigowa. A kausashe ta kai dubanta tana nuna shi da yatsa tare da faɗin "Kulll ba'a katseni idan ina kan magana ta" Ta faɗi tana me ci gaba da faɗin. "Tun daga loƙacin dana fahimta ina ɗauke da cikin dake jikina nima se nawa hankalin ya kwanta amma kullum kwanan duniya da tunanin yadda zan ɓarar da cikin jikin wannan la'antacciyar nake" ta faɗi tana nuna Jadderh. A kausashe AK ya miƙe tsaye tare da watsa mata wani kalan mugun bahagon kallo na zakici ubankine. Kafin a zafafe ya furta, "Shedar ke ɗin ba komai bace face dabba. Ki sani kowa yana iya zuwa yai farauta! Amma ba kowane wanda ya iya farauta irinta damisa ba!!!.... Shi kaɗaine wanda aka aifeshi da tambarin farauta a cikin zuciyarsa!. "Kaiiiiiiiii!" Moh ta dakama Ak wata uwar tsawa tana sake juyawa ta fuskanci moh "Amma duk da hakan ban samu kwatankwacin kulawar da jadderh ke samu daga wurin kowa ba wannan dalili ya sanya na haɗa kowa da kowa na musu kuɗin goro kowa na zana shi a matakin da nakeson ya kasance. A haka cikin irin wannan halin Jadderh ta fara nakuda me zafi sosae wacce ta ɗauki kusan Kwana tara tana yi nima kuma a cikon kwana na goman na fara tawa nakudar ɗakinta na kallon nawa haka na haihu na barta cikin halin ciwo da fita a hayyaci. Yara biyu na haifa duka maza masu masifar kama da juna sedai ɗayan bezo da raiba ina haihuwa norse bata jima da gama gyaraniba na jiyo kukan jariri a ɗakin jadderh, zuciyata a kaikashe na nufin ɗakin da niyar na kasheta na kashe abinta ta haifa sedai kallo ɗaya nama yaron naji ya banaso na kasheshi, inason ne na reneshi tamkar mahaifiya a gareshi daga baya kuma na bayyana masa ba nice mahifiyarsa ita kuma uwar na saceta bayan na maida mata ɗayan yarona da dama bezo da raiba. Ɗaya daga cikin amintattuna na kira nasa aka sace min ita xuwa cannn wani gourdsroom da aka denan shigarsa kwatata saboda irin abubwan da ake gani a cikinsa na al'ajabi. Babban tashin hankali iyaka tashin hankali waɗan nan family sun shiga barinma dangin jadderh da kuma shi me martaba marigayi. Tun yaran na jarirai na gane baya ɗaukar hussein se hassan..... "Dama kin taɓa ganin mutum yaso jinin daba nashi ba irindai soyayyar ɗa da mahaifi, ai wannan daban take Allah da kanshi ya faɗi hakan hajiya jiddoh" Wanna karon muryan jaddern ce ta karaɗe ploor'n. Kana taci gaba da faɗin "Dake a tunaninki soyayyar da uba ze nuna ma ɗansa zeyi kwatanci da wacce ba shine jininsa ba bare ma mu jininmu da duk inda yake a tafashe yake tafarfasa yake tamkar ruwan dake watstsara a tukunya, kuma ki sani tun daga loƙacin da kika shigo naji shigowarki hakan yasa nayi saurin kunna record a wayana har kikai komai kika gama komai na naɗe a cikin nan" Moh ta faɗi tana ciro wata tsohuwar waya irinta ɗa can ɗin nan ci gaba tayi da faɗin, "A naki banzan tunanin ke kadaice me wayo to ki sani Ashaan sai daya saurara komai dake cikin nan" ta sake faɗi tana nuna mata wayar still. "Fahimtar danai kamar akwai abinda ya sani dangane da hakan yasa na kawar dashi ba tare da anyi zargin komai ba, ni da hannuwana na sanya pillow na kashe shi tun yana shure shure harya dena. Kinga kenan ko a nan nayi tunani me ƙyau" Moh ta faɗi tana wani gyara zamanta mandood tsaye daga gefinta. Kana taci gaba da cewa "sedai bansan sanda ke kanki kika rayu har haka ba, shin ina allurar da ake miki?, ina likita oxwa yake? Shin tayaya kika tsirane ma wai Jadderh? Bayan duka uban matakan tsaron dana zuba Niki? ...... cikin wani kalan izzar daya gama mamaye jinin jikinta Jedder'n Ashaan ta furta. "Ta hanyar gwarzon namijin mazaje Jarumi a filin daga namijin damisa ne ƙwaya ɗaya tak daya tari gungun mayaƙa majiya ƙarfi masu ɗauke da manyan makamai!, TAKWABI Ɗaya tak da zaiyi zarra ya kwantar da dubban takwabban da suka zagayeshi sukai masa ƙawanya, har gaban Abada *ABDOUL-MALEEK HASSAN AL-HASSAN ASHAAN* shi kaɗai ne jarumi ɗaya tak a illahirin Masarautar EMAAR's damisar da aka haifeshi badon ya mutu ba sedan yaƙar maƙiyan papansa, shine shila buɗe ko wanne sabon babin taɓarɓarewar rayukarki Jiddoh. Kince naci amanarki zanso ki tuna ni dake waye yaci amanar woni! Kodan dama masu iya magana sukance bishiyar da aka dasata domin Allah tafiyin Rassai. Karki manta keda iyayenku duka cin arziƙine ya kawoku ƙasar makka a haka har allah ya haɗamu daku sanadiyyar aikinku. Na ɗauke ki tamkar ƙawa ƴar uwa tamkar Lajja haka na ɗauke ki, Nawuce miki gaba har nasa Pappienmu ya sanyaki school boko da arabic. Min tashi dake tamkar ƴan uku rana tsaka bayan gama sanin sirrikanmu da kikai kika rabani da Ashaan a loƙacin ba shine sarki ba. Kin aauremin boyfreind nawa na haƙura na ƙyaleki, a rayuwa kinyi min abubuwa da yawa duk na dauke ido na toshe kunne amma duk acikin wannan labarin dai ni ce maciya amana? jiddoh" Jadder'n ta faɗi tana me duban moh ɗin da jikinta ɗauki rawa tun a farkon kirarin da tama AK. Tabbas idan tace bata ji tsoro ba to kusa tayi ma kanta ƙarya, don wani kalan tsoro ne ya lulluɓeta nan abubuwan da suka faru shekarun baya suka shiga dawo mata daki daki, take tsoro da firgici sun mamaye zuciyarta, sakk waɗan nan kalaman sune furuci na ƙarshe daya fita daga bakin Ashaan a wancan loƙacin sedai banbanchin suna kawai da aka samu A maimakon *ABDOUL-MALEEK* shi *HASSAN AL-HASSAN ASHAAN* ya ambata tabbas iri ɗaya ne maganar ko tantama batayi. Bata gama dawowa a hayyacinta ba ta sake jin muryan jadder tana me ci gaba da faɗin, "Daga ƙarshe ma ƙasar na bari na koma wurin Nenne Alayya bnt zubr da zama a ƙasar luponia. Amma dake bawa be isa yanke hukunci ko zartat da abinda Allah beyi niya ba to kuwa wani bawa be isa aikata shi ko hanashiba, kwasan se ɗaurin auren mu kikaji. Rabon se wannan me gurbin tazo tayi nata yaryaɗon kana bi diddiginta zataci albarci, tunda dama shi haka me cin arziƙi yake duk inda yake da wuya beci amana, shi yasa temako yay ƙaranci, sabo da irinku kuke ɓata na gari duka kusa a hadeku a muku kuɗin goro. Wanna tsayayyen namijin da kika gani gabanki shine maganin kukana dama duka sauran alhlin Emaar's don haka go dn way tun kafin loƙaci ya ƙure miki. ★ ƙattan mazaje ne guda Uku majiya ƙarfi tsartsaye a bakin Kamfacecen parlor'n na alfarma, ko wannensu sanye cikin shiga irinta kaka gida hannuwansa riƙe da manyan bindugu, A hankali a kuma sanyaye ya fito cikin kamala da kuma nutsuwa kallo ɗaya zaka may kaji ya shiga ranka farat ɗaya, ASAAD EMAAR's kenan shine ɗa na biyu a wurin moh jiddoh. Kuma shine halayyarsa da nata suka sha ban ban tun daga yarinya, tunda ya fito wannan mutane ukun suka mara may baya. Kai tsaye waɗan nan masu ɗamarar ya fara sallama yace musu suje kawai wannan ɗin aikin cikin gidane kuma zasu magance matsalar da kansu. Amma suka ce dole se sunga moh suna shiga moh ta saki wani kalan kayataccen murmushi tana me furta, "Bismillah ku ƙaraso ga mai laifin ma se kuyi ramm dashi!" A maimakon taga sun kama Ak ɗin sema wani kalan zaro idanuwa da sukai duna sara masa. Jikin kowannensu na rawa don magana ake *_A general Soldier's nd police Inter pool *_Special anti terroRism squad_* *_Security squad group_* magana ake ta *~💸 THE BILLIONAIRE 💸_ABDOUL-MALEEK EMAAR's KUWAIT_* wanda kafff duniyar ta sanshi sedai ba fuska da fuska ba. Kallon kallo aka shiga tsakanin mutanen ɗakin da hannu AK ya musu alamar su fice a ploor'n. Seda suka sake sara may da wani irin salo suka juya suna barin masarautar ma baki ɗaya. "Da naso daga ke har ƙasusuwan bayan naki zan haɗe na ƙarasa ɓallewa amma sedai cin zarafin mutum ba'a cikin jininmu yake ba, Amma sedai kin ɗanyi kuskure kaɗan mutuwar Grandpaah ba'a hannunki take ba dama can Allah yayi a ranar zebar duniya donke baki isa kisan merai ba" Ta cikin systerm ɗin da jearah ta ƙira Zaid video call suka jiyo maganar zaid ɗin tamkar daga sama. Ak ne ya dubi zaid daga inda idanunsa yaɗan lumshe tare da buɗesu cikin wannan dakakkiyar muryan nashi ya furta. "Ka taɓa ganin inda mutum ya aikata lefi ba tare da an hukuntashi b@!?. Dole zasu girbi abinda suka shuka da hannuwansa zaid se sun ɗanɗani rayuwa a inda Haskena tayi,ni ban yafe ba ko kowannensu ya yafe dole ni na hukuntasu" Shigowanta kenan ta furta "Ba kaine ya chanchanta daya hukuntasu ba Garga! Dama duk inda gidan sarauta yake gida ne mai ƙunshe da halittu iri daban daban, wanda ido ka iya gani dama wanda idanuwanmu bazasu iya gani ba, duk inda gidan sarauta yake babban gida ne wanda komai ka iya faruwa cikinta, dik yanda aka ce maka akwai mulki da sarauta toh zai matuƙar wahala ace babu zalunci sai waɗanda Allah ya kiyayesu!. Wasu mutanen sukan nemi mulki da sarauta ta duniya koda kuwa zeyi sanadiyayyar rasa ransu. wasu mutanen babu abinda bazasu iya ba domin kawai suyi mulkin. wanda wasu mutanen ma shi wannan mulkin shine zeyi sanadiyyar shigarsu wutar jahanna. Annabi muhammad (S'A'W) yace mana duk wanda aka be wani muƙami koda kuwa na monitor ne a cikin class to tamkar an ɗauki mukullaine guda biyu an ɗamka masa a hannunsa, wato mukullin gidan wuta dana gidan Aljanna idan kayi alhairi kanka idan sharri ma kanka kaine ka zaɓa mukullin ƙofa ɗaya a cikin wannan mukullan inma *WUTA* inma *ALJANNAH* don me yasa mutane bazamu ringa tuna lahirarmuba a kullum kwanan duniya babban burinmu shine mu samu duniya a hannunmu don haka duk abinda mutum ya aikata kunyar kansa kuma ka barshi da fitowar rana da faɗuwar tama wani babban jafainne, Allah kaɗai Allahu samad shine maganin duk wanda yake jin yakai ya kuma fi ƙarfin kowa to kuwa tabbas Allah shine zaiyi maganinsa ya kuma ji tsoron ranar da zasu gamu ranar da babu gudu babu ja da baya kowa ze amshi sakamakon abinda ya aikata anan gidan duniya. Wasu rashin wayo da aiki da hankali kan jawo su faɗa tarkon mugu! Sabo da sammm Shi mugu idan ya cika mugu ai baya bayyanawa duk mugun da ya baiyana kanshi bai cika muguba. kuma alhamdulillah Insha Allah sunyi ta bayyana kenan bawai iyaka moh ɗin bace..." Oum tayi maganar idanunta akan AK Tsitttt kowa yayi a ploorn inda jikin wasu daga cikin masu baƙar zuciya amma tasun bata fito filiba yay sanyi ga son cutatar da ƴan uwansu, wasu kuma ko gezau dama jikkunansu beyi ba bare suji abinda aka faɗi ɗin. Asaad Emaar's ne ya dafa shoulder na Ak kai ya jinjina may alamun yabi yacce oum ɗin ta faɗi. A fusace Moh ta miƙe tsaye tare da furta "Kenan kinyi nasara a kaina kenan jadderh?" "So kike na sake maimaita miki da baki cewar naci NASARAR ne? Dan nasan ke a karan kanki kinsan cewar naci nasarar! Tunda gashi GUDUN ƘADDARAR da kikay tayi tazo ta sameki har gadon baccinki, kuma gashi kin buɗi ido kinga masarautar Emmar's cike take dammm da JININ JADDER'N ASHAAN ɗin da baki so ba kuma dama ai ɗaurin talala Ubangiji ya miki kuma ki iya bakinki don har yanzu akwai wani babban sirrin da ban bayyana shiba daga gareki! Idan kuma kikace zakici gaba da wannan haukar to kuwa tabbas zaki sha ƙasa, ki sani Inda ba yashi nan ake taƙaddamar kokawa. Kuma shi ramin ƙarya kurarrene in kuma zubawar kikeso ayi to mo zuba mu gani!!!." Jaddarh tayi maganar tana mikewa da shirin palon ploor'n baki ɗaya. "Wllh baki isa ba. da baki mutu bama yanzu ciwon zuciyar mashayen jikokinki zay karasa kasheki Jadderh, don wllh ba'ayi mutumin da zaici nasara a kaina ba ni jiddoh kuma harya zauna lafiya ba'a haifeshi ba, dagake har jikan naki da kike ganinsa kamar wani malaikan mutuwa senaga bayanku kwarai" Cakkk jadderh ta tsaya tare da juyowa kafin ko tayi wani yunƙurin yin magana jesrah charaf ta rigata. "Ashe baki sadudaba jiddo wai bakiji abinda tace miki ba kar allura ta tono garma fa ahammm" Zaram Hussein da ya dade da zama statu a wurin ya chafki hannun jesrah. Kaɗe hannunsa yajj anyi Ak ne tsaye a kansa. "Mafi munin kuskure da zaku sake aikatawa shine ɗayanku ya sake koda yunƙurin taɓa ɗaya daga cikin family nane wannan shine kuskure mafi girma da muni da zaku zake aikatawa" yana faɗar hakan ya wancalar da hannun hussein ɗin yana barin wurin baki ɗaya domin a halin da yake ciki jiyay jininsa na wani kalan mugun tafarfasa ta ciki. "Duk bana bukatan wasu sauran maganganu haka nan, mashaya kuma da kike magana karki manta mahaifinki tirela² yake siyarwa. Kuma ganan a karkashinki suma da kika zama sanadin yinsu Insha Allahu zasu dena da ikon Allahu ahaad" Daga haka tasa kai ta fice gaba ɗaya daga ploor'n wani shegen murmushin gefen baki lajja tayi tare da tsayawa a gaban jiddohn, "Kinji ai abinda ta faɗa miki ko a yanzu itace tayi nasarar lashe wasan da dama itace hasalin ƴar wasan. Dan se a yanzu na tabbata lallaie tafashashshen jinin mu shike yawo a jikin duka wadan nan family. toya kika gani? A dama da take ita kaɗai bakiy nasara akantaba bare yanzu da take zagaye a jikin matasan zakuna masu farauta, Idan kuma kikace zakici gaba da waɗan nan abubuwan to tabbas *KAREN BANA* ne zeyi maganin zomon bana idan har baki manta ba ai nasha faɗa miki haka dama moh... Daga haka itama lajjan tasa nata kan ta fice haka kowa ya shiga ficewa, ana barin moh da iyalanta Al-hussein kuwa tunda moh ta fara bayaninta ya zama mutum butumi, don besha makirci da rashin imanin mahaifiyarsa yakai har haka ba, besha zata iya kisan rai koma yace rayuka ba. Kenan itace ta kashe musu mahaifinsu? Ita kuma mijinta lallai sema yaji duniyar tana ƙarasa fice masa akai. Kallo ɗaya umaymah ta jefama moh ta ɗauke kanta tana ficewa takai ƙofar ita kenan tajiyo muryan moh na faɗin. "Kema saura ke tunda naki asirin be tonuba! Na tabbata ke idan sukaji kene wacce take poisoning na mahaifinsu to ke saidai hukuncin rataya kuma umaymah. Cakkkkk ta tsaya tare da juyowa "Ke kanki kiji da wutar gabanki keda sakaran ɗanki mara amfani idan ma kin sake buɗar ido kin ganni a masarautar kenan. gadai jikanki nan mandood na barmiki yasmine kuwa dama jininku bace jinin turawace don daga kan mandood ya kasa bani wani cikin duk kuwa da yadda nake maitar haihuwar kodan na gaji dukiyar masarautar nan. Daga loƙacin da kika riga kika bayyanamin cikinki tun daga loƙacin na fahimta nayi kuskure na shigowa wannan masarautar ta hanyarki, tunda kema karerece a karere kike keda jikokin naki, don haka banga amfanin zama da marasa amfani ba nikam na ƙara gaba dama wannan ranar nake jira kuma tazo don haka na tafi mebi forever mebi kuma not...." daga haka taja hannun yasmin (Dolly'n Salman😂😁) suna barin palon suma. Moh, Al-hussein, mandood, Assad,Asiaa (Matarsa), mahboob, duka da kallo suke bin bayan Umaymah jikin kowa a mace a sanyaye. Wasu zafafan hawayene suka kwaranyo daga idanun Alhussein, kenan duk zaman zamanin nan amfani kawai mahaifiyars da matarsa sukai ta hanyar cutatar da waɗan nan bayin Allah?. Lallai seyau ya sake yarda tuggun mace duk ƙanƙarta ba kanwar lasa bace, "Innalillahi wa'inna ilaihir raji'un!!!" ya shiga maimaitawa Assad ne yay ƙiran woya daga bakin get yace duk wanda suka gani karsu barshi ya fita ko waye kuwa. Daga ɓangaren umaymah kuwa uban tulin dukiya da suka take a wasu manyan trolly lugage suka ɗiba tare da fitowa da niyar su fe ce, sedai me suna zuwa tun a get na farko akai ramm dasu.... *NIGERIA KANO* ★ _Kamaal_ zaune yake saman chiar system na shi ajiye saman desk se wasu ƙananun glass cup yana opreting,tshirt ce mai gajeran hannu a jikinshi haɗe da short. Idanunshi a sakaye cikin glass ya zuba su akan system ɗin shi da yake famar aikinshi akai.gefen sa Marie ce kwance tana sanye cikin riga da wando,kanta babu scaf anyi mata space buns,se wasu baby ribboms data saka akan nata gwanin birgewa ɗan matashin cikinta ya sake fitowa dass dashi daya mata kyau sosae. Farkawanta yay daidai da kammala aikinsa side hug yayi mata yana ɗan rungumota jikinsa..... *BY AMMEY LAYLERH👌👍* *🦅 MIKIYA 🦅* _A wonderful world & Special anti terroRism squad_ ____________________ *MARYAM NASEER MIRRAH* ~AMMEY LAYLERH ✍️~ ✯ *~🌠 JAJIRTATTU WRITER'S ASS.... 💫~* BOOK Two…………………………񆬍✍ 31&32 *Bɪꜱᴍɪʟʟᴀʜɪʀ Rᴀʜᴍᴀɴɪʀ Rᴀʜɪᴍ* ♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡ ★ _KUWAIT_ *EMAAR's* Assad ne bayan fitan kowa ya kalli Alhussein tare da faɗin "Alhussein yau dai ka yarda ka gamsu da abinda nake yawan faɗa maka ko?". Cikin yanayi gamsuwa Alhussein ɗin ya kalli ƙanin nashi tare da gyaɗa mishi kai.Shi kuwa Asaad a nitse yace. "Dama nasha gaya maka kai ɗin sha giri girbaune wautace kawai ke damunka irin ta ƴaƴan fari da ƴar hasada, sannan kuma da zugan wannan wannan shegiyan matar naka me zubin angulu da kan zabo, Ni kaina yanzu na fara tamtamar anya kuwa moh itace mahaifiyarmu ta gaskiya ba satarmu tayi ba?.". Yayi maganar yana kallon ɗan uwan nashi "Ahar kullum karka manta waɗan da moh ke ambata mana a matsayin wadan da sune suka kashe mana mahaifinmu" Da sauri Alhussein ya gyaɗa kansa.Yayinda shima mandood da mahboob ke tsaye suka zuba ma mahaifan nasu ido. "Kayi shiru Alhussein ita rayuwa kowa abinda ya shuka zai girba, kada ka wani tada hankalinka sosae don ada tun loƙacin da muka fara binke na sirri a cikin masarautar nan nida zaid da kuma Ak.kasan da muka tashi bamu tsinci kowa a cikin magautan masarautar ba daya wuce Moh mahaifiya a gare mu!, wllh a loƙacin wani kalan kunyan yaran nan ne ya kamani sema naji na muzanta a take. Amma haka yaran nan tamkar sune yayyun nawa suka ta bani kwarin gwiwa da haƙuri, se nayi koƙarin zare hannuwa na a cikin lamarin amma se suka gwada min kawai suma zasu dena na, sedai abu ɗaya da mu duka yafi jan hankalimu bayan mun gano moh ce tsamo tsamo ta ko ina ta kanainaye shine yawan ambatar sunan *JADDER'N ASHAAN* ɗin da take. Tare da *EASHERH* haka mukaci gaba da bin diddiginta har muka gano ashe ba itace mahaifiyar Paah ba kana ga yarinyar sa ta fari da tayi sanadiyyar ɓacewarta ɓatt. Cikin sanya idon camera's din da duka muka sanya mata haka har muka inda asalin wannan Jadder'n Ashaan ɗin take, daga nan ne na sanya AK ɗauketa ya mayda ita keɓantaccen wuri kafin xuwa wani ɗan loƙaci. Duk wani shige da ficen ku a loƙacin a tafin hannunmu kuke har kamo loƙacin da kukaso sake kawar da Paah a karo na biyu. Babbar sa'arka ɗaya da duk yunƙurin kisan da ake masa ba tare dakai bane kai kawai kurarain ka iya da hargowa kuma dama tuni muka gano Dolly ba ƴarka bace cikakkiya. Har zuwa loƙacin da matarka taso cutar da *ABDOUL-MALEEK* ta hanyar jefashi ƙaidin zina amma kuma se Allah ya kare shi ta hanyar kawo may matarsa har inda yake. A yanzu haka umaymah na tsare a hannunmu sakamon tattalin arziƙinka data kwashe kamar yadda tayi ikirarin barinka, tabbas zata barka ɗin amma ba tare data fita da ko kwabon kaba. Kuma ka sani nida kaina seda nace se an hukuntaku amma AK yace ai ana barin halas ko dan kunya wllh bansan da abinda zan sakama waɗan nan mutanen ba sedai muci gaba dabinsu da fatan alhairi, da kuma adda'ar Allah bayyana mana duk wani ɓoyayyen mugun dake cikin waɗan nan masarautar kamar yadda *MARYAM* ta faɗi. Zuwa wannan loƙacin hawayene kawai ke zarya wa fuskan alhussein na tsananin ladama da dana sani mara amfani. Da hannu Asaad ya yafito Adeenerh da rarrafe ta matso gyaraeshi tana jan ijiyar zuciya idanun nan sun kaɗa sunyi jajir tamkar wacce tayi atishawar tsaƙi. "Adeey ki yafemu ki yafemu bansan da wanne irin baki zanyi amfani wajen baki haƙuri ba, saidai kawai nace Allah ya baki haƙuri Adeey!!!" Dake haka yake kiranta tun tana ƙaramarta, kuma dama wata shaƙuwace ta musamman se kuma daga baya yabar ƙasar ma baki ɗaya saboda wasu mugyayen halayen mahaifyarsa. "Yaayaa bakumin komai ba ni!, kawai ina kukan tunawa da Mahy da nayi ne duk da kasancewar ban santa a zahiri ba se a photo. Amma ina ƙaunar mahy ta ina sonta kuma ina kewarta sosea wllh" "Moh ta zalinceki ta raba ki da mahaifiyarki da ko saninta bakiy ba kum...... "Allah ne ya ɗauki ran mahy ba moh yaayaa kuma shi ɗan adam aduk inda yake ajizine, ka ɗauka hakan a matsayin ajizancine da kuma ƙaddararta dama Allah ya nufa zata mutun!kuma a ranar a loƙacin sedai kawai ace itace sanadi kasan ance duk abinda ya faru da bawa dama hakan yana cikin tarin ƙaddarorinsa sedai wani ko wata su zama sune sila" Ta faɗi hakan wasu hawayen na sake kwaranyo mata bayan hannuwanta ta sanya tana sharewa. pamp na gadon bayanta ya shiga shima idonsa na cika da tausayin ƴar uwarsa. Tashi tayi tana bin bayan grandpaa ɗinsu itama jikinta a matuƙar sanyaye ashe moh itace wacce ta rabata da mahaifiyarta tun tana tsummar goyonta. * Suna shiga palon queen lajja tamkar wacce aka tunasar da ita iyayen nasu ta jawo wayar ta data manta a ɗakin da suka sauƙa, kai tsaye lambar mahaifinsu ta danna ma ƙira don se a yanxun take tunowa ashe fa tunda abin nan ya faru babu da wanda tayi waya tsabar murna da kanta daya juye. Sheik Aliyullah Dawood kuwa yana kingide daga jikin *KAABA* yaji ring na woyarsa cikin nutsuwar da yafa fara tafiya da tsufa ya ɗagawa wayar tare da karata da kunnensa sosae. "Assalamu alaikum Ya habibullah! Alhamdulillah Alhamdulillah Alhamdulillah Allahu Akbar JEDDERH! JEDDERH!! JEDDER'N ASHAAN, JEDDERH ALIYULLAH DAWOOD!!!" Ta faɗi tana jin yadda halshenta ke ƙoƙarin karyewa wajen ƙarasa bayanin, hakan ya sanyata dakatawa tana fesar da wani cukuykuyayyen numfashin daya maƙale mata. Cike da kaɗuwa Sheik Aliyullah Dawood dake kishinƙiɗe ya miƙe zaune daram tare da gyara zaman wayar a kunnensa sosae. Wai ko gizau ɗin da kunnuwan suka saba masa ne yau ɗin ba suka may, Amma sake tsinkayo muryan Queen lajjan na sake faɗin. "Alhamdulillah Habibullah Jeddeenmu ta dawo Habiey zatonmu da tsammanin mu ya zama gaskiya jeddernmu ta dawo gata gabana Habiey kace Alhamdulillah" "Alhamdulillah!!!²" yashiga maimaitawa tare da ambatar "Ta mutu ne da ciwon rashin tabbacin ɗiyarta na raye ne ko tana mace! Ta mutu ne da ɗacin zuciya da zafin rashin sake ganin gudan jininta tun daga randa ta miƙata ga Ashaan, lallai ta tabbata kenan komai ya bayyana ɓoyayyar ƙarya ta koma gaskiya ta bisneta bani ita *EASHERTOUL HUMEIREH" A kuma daidai loƙacin ne jedderh ta yanke jiki ta faɗi kasancewar muryan abin ƙaunarta mafi soyuwa a gareta da taji, sosae taji kanta ya wani irin balain sara mata don dama bawai ta gaya zama normal bane a sannu sannu brain nata ze zama fresh babu damuwar komai. Cikin wani irin yanayi lajja ke kallon jedderh dake kwance jikin Hassan Al-hassan ashaan daya tarota ta faɗa jikinsa.Cikin wata iriyar murya mai raunin amo AK yakai gwiwowinsa ƙasa yana kamo hannunta murya na rawa yace. "H...Has..Haske naaaaa" ya furta tare da amsanta daga jikin mahaifin nashi yana maida ta jikinsa tare dajan goran ruwan dake gefensa ya shafa mata daga fuskanta zuwa wuyanta. Wani wahalallen numfashi taja tare da ɗago jajayen idanunta da tsananin ciwon kai ya rinasu ta sauƙe akan *AK da ME MARTABA SARKI HASSAN AL-HASSAN ASHAAN* kan ta riƙe tare da ɗan jujja kanta kana ta saki murmushi tare da faɗin. "Alhamdulillah! Alhamdulillah!! Alhamdulillah!!! Yah Allah na gode maka bisa wannan rahama da kaimin ko yau ka ɗauki raina burina ya cika, yau gani ga gudan jini na zagaye da ahlinsa cike tabb da familyn Ashaan cikin masarautarsa Allah ya cika may burinsa na ganin tsatsona sun zagaye wannan masarauta, ta ƙarasa faɗi wani irin kuka mai rauni da cin rai na kwabce mata. Adeenerh dake bakin ƙoface ta rarrafo tana faɗawa jikin jedderh tare da fashewa da wani irin raunataccen kuka. cikin kuka ta tattaro duka kan mutanen ɗakin tana me faɗin. "Ba kuka ya kamata muyi ba wannan loƙacin dariya da farin cikine Kaku's kunzo duk kunsa munata asarar hawayenmu akan wani tsoho can daya rigamu gidan gaskiya ma yana cen yana hutawa abinsa" baki ɗaya kuka da dariya suke duka loƙaci da mazansu da matansu suka haɗu duka sukama ma jeddern ashaan ƙawanya suka mata zobe tana tsaƙiyarsu. Tare da Mahaifinsu da shikam baya da bakin magana samm se aikin sharce ruwan hawaye yake na farin ciki da akasinsa. " *AH!MINHR* me yasa suka rabani dake? me yasa basu bari ko cikakken numfashinki na shaƙaba ? Duk miye dalilinsu na yin hakan MULKI?, ko kuma DUKIYAR dake cikin EMAAR's nasan duk wani Harmutsi akan dauɗar duniya akeyinsa wato *KUƊI RIKICIN DUNIYA* kenan don duk wani rikici na duniya tun zamanin da can can ma akan kuɗine wanda ake ma laƙabi da masu gidan rana. Adeenerh ce ta sake komawa jikin jedderh ta maƙaleta se kace wota mage. "Iyyeeeeeee kaga wani ƙasaitar biko tsarki da romo to ɗaga min twin na karki karyamin ita tun kamin habiey ya ganta" lajja ta faɗi da murmushi a kan fuskarta Razeenerh ce tace "Yo Oum asha anun ganin arhar gabas karuwa da sallar walha mana, taga cinya ta bati da ai anawa taƙe maƙalewa don haka ki hutarki my first born!" Anne ce tayi murmushin itama tare da kallon lajjan tsananin soyayyar uwarta na sake zagayeta tace "Oum Eash duk ƙyalesu su Didi ciwon baki kawai suke son sakamin kene kawai" ta faɗi tana komawa bayan lajjan don wata uwar harara da taga Zeenerhn na antayomata. "Didi ni!!! Ko kin zaɓi Maamah lajja kenan a akaina? shike nan bara nima ki gani na ƙira su Asha Anum kika yadda hasalin soyayya take" ta gaɗi tana kunna detar woyanta amma kafin nan seda ta ƙira ANUM ASHA kana tace ta hau online, se gata kuwa ɗoɗar a online ɗin video call ta ƙiranta tana zaune gefenta house maid's ne suna sarving nata abinci. "Zanyi magana da asha anum kawai" Mah ta faɗi. kai tsaye anum ta miƙe tana nufar bedroom nata don tasan me hakan ke nufi tanason ta keɓancene. Zama tayi saman lafiyayyan bed nata tare da furta. "Hiyyyyy! Mah kin riƙe mana su lajjanmu ko tun ana ɓoye ɓoyen fitarsu harma gashi kowa ya sani a halin yanzun" Mirmushi mah tayi tana me sake tabbar da mugun kamannin da ta gani ga meerah tare da anum ashan. "Kin gani sarkin ƴan surutu idan kinso leƙo ki ga nan nida wannan Anour ahliey ɗin wacce kikafi so?" Ta maida akalar video'n zuwa ga Anne ai da sauri ko wannensu ya shiga mirza idonsa. Bakinta da jikinta har rawa suke wajen furta "M....Ma..h!!! Wannnan kuma wace ce? Did ɗin kice? Dama shine dalilin fitar su lajja" se kuma ta yanka a mugun guje tana yin apartment na iyayenta. Da gudun ta shiga ƙiran "Abiey! Abiey!! Abiey!!!" Fitowarsa kenan da shirin fita wurin aiki suka kusa cin karo da ashan da rabon yaga dariyarta ma harya manta. Hannunta ya riƙo yana daidaita tsaiwarta da kyau kan ƙafafunta. "Anum Ash kina lafiya kuwa?" Tambayar daya jefa mata kai tsaye kenan. "Abiey kalla kalla kalla kaga nan wa ce ce wan nan?" Cakkk ya tsaya a loƙacin da idanunsa suka sauƙa akan Anne dake cikin wayar har yanxun tana kallon ikon Allah. "Me....me..Ea...sherh!?" Ya faɗi a rarrabe jikinsa na ɗaukar rawa zuciyarsa na dunƙulewa wuri guda. "Did...Didice di di ce JALAAL Ash!, Easherh Ash ce Autar lajja da Ash ce ta bayyana ta dawo garemu jalaal Asha" muryan mah ya sake karaɗe dodannin kunnuwansa. Wayar ya amshe a hannun Anum "Eshern Ash anum Easherh Allahu gafurum raheem! gaskiyar ta fara bayyana kanta kenan zeenerh ash" Ya faɗi cikin zumuɗi da gan ɗoki komai ya gama bayyana Jalaal ingo nan ma" Ta faɗi tana sake juyar da wayar zuwa ga *JEDDER'N ASHAAN* ai da wani irin suuuufa ya tafi se gashi jikin railer idanunsa woje bakinsa nason furta koda wata kalmace amma yaji ya masa nauyi da ƙyar kamar an fusga maganar daga bakinsa ya furta. "HA.. BEB....TIEY NOUR?..... Ya faɗi a rarrabe "Abtieyya Horoul ayn JALAAL" Kai tsaye ta sake tabbatar may da hakan ta hanyar ambatar sunan da yake ƙiranta dashi. Ɗif ɗif se ƙarar katse ƙiran suka ji. Ko ta kan anum asha be biba kai tsaye ya nufi fita yana wata wayar. Ata ɓangaren su mah kuwa tananin ƙaran datse ƙiran ta furta "Se ya zo kenan" ita dai Anne ido ne nata don kullum waɗan nan mutanen da sabon kulle kan da suke zuwar mata, Sallar zuhr kai tsaye mazan suka fita su kuma matan sukayi tasu a gida. Tate da Jalaal Ash sukayi sallar zuhr ɗin gaisawa aka shiga yi fashi. Yau kam sakamakon ɗaure masa fuska da me marta ash yake masa ƴan kwana kin nan sakamakon wani ɗan saɓani daya gitta tsakaninsu se yaga saɓanin hakan. Don kuwa da wani tattausan murmushin farin ciki ya tareshi yana ta mai maita Alhamdulillah. Haka suka sake ɗunguma xuwa pary ɗin dasu Lajja suke faka faka aikin sauri JALAAL ASH ya shiga aikin harhaɗa kansu don yace a yau ba se gobe ba se sun dire da Makka ga Sheikh Aliyullah. Ya buɗe baki kenan da niyar sake ma mah magana akan tace ya bari zuwa washe gari mana sannan sun ɗaɗa hutawa maganar ya maƙale sakamakon ido biyu da yay da meerah. Da hannu ya shiga nunata yana furta "Asha? Yaushe na fara wannan wasan dake? Ashe ba zaki nutsu ba kenan ban hana ki yawo ke ɗaya ba? Ke banma ce karna kuma ganinki woje ba ko...... "Maraeymah babbar ƴa ga EASHER ASH kenan kaima kaga ANUM ɗin kenan?" Da wasu kalan idanu ya shiga bin lajja dasu da tayi maganar se kawai yakai goshinsa ƙasa yana fashewa da kuka. "Yaaaa ALLAH! Kai ka san nufinka na karkasa Wannan ahali gashi kuma ka haɗe a sanda kaso! Me bi zaman mu a tare muyi rayuwa ba alkairi bane ya wadud komai idan ka zartar a kanmu me kyaune sede muce Alhamdulillah!!!" "Ida ɗin mata ce ga *ABDOUL-MALEEK* ɗan daya kasance jika a garemu *HASSAN AL-HASSAN ASHAAN* ɗane ga Jedderh wanda ta haifa aka musanya mata da matacce Allah yayi loƙaci ya kawo bayyanar gaskiyar lamarin dake ɓoye". Wannan karon Mah ce tayi maganar "ALLAHU AKHBAR" Jalaal Ash ya sake maimaitawa da ƙarfi sosae yana haɗe Annen da jedderh da kuma Meerah duka ya rungumesu yana sake sakin woni kukan. Wani kalan farin cikin daya jima beyi ba na sake mamayarsa. (Kunsan dai al'adar larabawan nan haka nan suka babu ruwansu uwa ta rungume ɗanta lol karku wani damu😂😁😀 nasan wasu bakinsu seya gaza shiru suce wannan AMMEYLAYLERH ɗin kaza da kaza to duka na biku naaaaaaa😷😱😨😯 babu luwana banyi zagi ba ko MY LAYLERH?😑) Dole babu yacce suka iya babban ɗa ga lajja ya kwashi ahlinsa suna ɗagawa zuwa makka, bayan ya ƙira duka sauran ƴan uwa na kusa dana nesa ya sanar musu wannan babban abin farin cikin daya same su. Ai kuwa kusan kata faninsu gaza haƙurin washe garin da jalaal yay musu alƙawari sukai se gasu a makka don gani suke goben tamkar shekaru dubuce daga can makka ma duk wasu ƴan uwa sun gama hallaruwa tun kafin sauƙarsu kasancewar wayace wannan bugama wancan wancan buga ma wannan tuni katafarin gidan Sheikh Aliyullah Dawwod ya cika. Makil da ƴan uwa na kusa dana nesa. Hardasu iyayen su *JADDA'N MALEEK TOUFIQ* da iyayen *ALIEYONMU* ashe duk ƴan uwan juna suke amma *JADDA'N MALEEK TOUFIQ* ɗin bata zoba ta cikin littafin AMMEYLAYLERH na *KAREN BANA* , shi kuwa dama pilot *ALIEYO* yana a ƙasar ne tare da my *JAAN* tashi wato FATEEMERH ALMUSTAPHA WAZEER dinmu. Ta cikin littafin *ƘAUNA BIYU* na AMMEYLAYLERH lol. *NIGERIA* _ABUJA_ *Salman pov* Zaune yake cikin tantiran abokansa na ƙunyiyarsu na gang bang. Cikin yaƙini amma kuma da yanayin damuwa yace. "Nanda wata uku masu zuwa zan koma ƙasar *KUWAIT* zanyi yaƙin neman *MEERAH* koda kuwa zan rasa rainane zan koma gareta domin ganin ni kaɗainane na mallaketa, kana kuma na gaya mata har abada da sonta zan mutu kuma shine sanadi don wllh da zuciya ɗaya naji ina ƙaunarta" Cikin bashi ƙarfin guiwa ɗaya daga cikin abokan nashi yace. "Zama kayi nasara Insha Allahu dud" A hankali cikin abubuwan da yake haskowa ya furta. "Babu tabbas dud duba da ganin cewa komai ya gama bayyana kansa ita kanta yarinyar ashe jikace ga sarkin madina kana uwarta ƴar haifaffen wannan shahararren malamin limamin makka ce wato SHEIK ALIYULLAH DAWOOD ce da wuya nayi nasara kasancewar mijin data aure ba tsarana bane amma zan gwada sa'a ta domin baya taɓa yanke tsammani daga abu idan har ita ɗin rabo nace zata dawo gareni"... Daga ya tashi yana fita don zagaya ketafaren gidansa dake Abuja wanda su abokan ne suka fito dashi da taimakon abokinsu dake aiki amma bawai bellinsa akai kai tsaye ba a matsayin wanda ya gudu ake nemansa. Abinda Ya faru kenan. ★ *Zaid pov* Bayan kammala saurara da ganin komai da yay ne ya miƙe cikin tafiyarsa na mazaje ya nufi ƙofar fita, yana fita compound na gidan arms ya ƙaraso da sauri don ganin kamar fitane zaiyi ma. "What's wrong with u?" Arms ya jefa masa tambayar don ganin kamar yana cikin yanayi na damuwane, jin gina yayi da jikin Railer yana rolling ƙafafunsa tare da fesar da wata iska me ɗan hucin zafi ta bakinsa. Tare da furta "I miss your country ne kawai Arms!" "Wani abu yana faruwa ne ata can da baya tafiya daidai?" Arms ya sake tambayarsa don yasan akwai abinda ya farun kenan, "Komai be faru ba sema abubuwan murna da suka zagaye mu ata dalilin matar Twin" Zaid ya faɗi fuskansa na ɗan sassautawa. Ma'am merrah kenan?" "yeah ita fa grendmom nata nd my J...nmu he is my IDENTICAL TWINS ne" yamai baya nin a takaice don bayson wani surutu me yawa haka nan yau ɗin. "Ikon Allah baya taɓa ƙare wa ya Rabb muma ka bayyana mana dangin my Mum tamu" Ya faɗi idonsa na ɗan cikowa da ruwan hawayen tunawa da mahaifansa da yay. "AMEEEN!" Zaid ya amsa yana fara zagaye compoun ɗin daga nan kuma seya koma ɓangaren gardena na gidan. ★ "Mr ayh bana iya tashi fa" mariey ta faɗi cikin kwaɓewar fuska idanunta a lumshe. "Ohhh god Rikicinki baya ƙarewa Mrs Ayh! Kince ke baki son komai se RUFAIDA YOGURD na kawo miki ganan kinsa har ya miki yawa kin hana ni sakat, Allah idan na kika yarda yau na rista ki babu me jinki bare kwatarki uhummm" Kamaal ya faɗi yana komawa zaune jikinsa sanye da kayan shan iska na maza pgmas ita ma sune a jikinta gaban rigar nan yay daga daga da abin Rugaida tamakar wota yarinyar goye. Kafafunya ta shiga yirzawa a ƙasa cikin wanda yay nisa a shogoɓa take tirza ƙafafun "to duk ba kai bane ka ɗaura min koma miye, Allah ban sake yarda dakai ayh" Sirirnkaran Hancinta ya ɗan ja tare da sakin wata siririyar dariya yana me faɗin "Tom shi ke nan mu gwada mu gani kona sati ɗaya ne haka" ya faɗi cikin dariyan mugunta don yasan hakan ma bame iyuwa bane,don tundata sami wannan cikin shikenan bata da wani motsi se nashi. Wani kukan ta sake saki tana faɗin "Duk laufin waye ba kaine ka fara kaini ga babban darasin ba ka barni a iyaka ƴar koyona mana, ni wllh ma seka goyeni kuma yau ka zaka min wonka" Wani kalan zaro idanunshi woje yayi yana faɗin "So kawai kike ki ɓallenine baby! Kalla kanki fa kin kusan biyuna a yanzu na tabbata" "Se dai dari kuma wllh wonka ba fashi uhummm kafin nan ma kuma se kamin tausa first" "Really?" ya faɗa tare da mata gwalo yana yin hanyar bedroom nasu da ɗan gudunsa. Itama miƙewa tay tana bin bayansa da ɗan gudu, akan bed ta same shi yayi Balance akan bed jikinsa ta faɗa tana chakulkulinsa nan ya shiga sakin dariya tare da mayar mata da martani daga haka kuma salon wasan ya sanja zuwa wani fanni na daban..... *BY AMMEYLAYLERH* *🦅 MIKIYA 🦅* _A wonderful world & Special anti terroRism squad_ ____________________ *MARYAM NASEER MIRRAH* ~AMMEY LAYLERH ✍️~ ✯ *~🌠 JAJIRTATTU WRITER'S ASS.... 💫~* BOOK Two…………………………񆬍✍ 33&34 # Hot Romance scene # Real life # Hot love scene # Ak meerah # A.k.a AMMEYLAYLERH👍👉 *Bɪꜱᴍɪʟʟᴀʜɪʀ Rᴀʜᴍᴀɴɪʀ Rᴀʜɪᴍ* ♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡ ★ *MAKKA* Tun kamin su isa airpot ɗin yake zagaye da wasu manyan fararen motoci na Alfarma da ƴan uwa suka zo taryan su Anne da jedderh. Kowa a ƙoƙarinsa nason fara tozali da jedder'nsu da kowa ya gama fidda rai da ita tare da iyalanta dake kewaye da ita. Dukansu ne a tafiyar ciki kuwa harda Ak da dashi yaso togewa seda oum tamay jan ido. Itama tare da ita Sarki Al-hassan yayi tafiyan, tafiyace ta sukayita cike da farin ciki da tarin nishaɗi. Jirginsu na yin landing katafanin ƴan uwa suka kewaye ƙofar saƙkowan kasancewar magana ake ta manya da manya ga kuma masu gidan ranar wato nera. Cikin masu tarɓar nasu kuwa harda Me girma Sheikh Aliyullah Dawood da kansa, tsaye yake hannunsa riƙe da wata farar sandan zinare daya ɗan sirka gold kolo. Yana sanye cikin wani tattausan farin yadi yalwatacce kansa naɗe da hirami kalan ruwan foda se sale salen baƙi. Idanunsa sakaye cikin wani yankakken farin glass don bema ido garkuwa daga faɗawar abubuwa maras kyau, A loƙacin daya sauƙe idanunsa akan jeddernsa zirrrr sega wasu hawaye na ziraro may. Jikin jedderh ne ya fara rawa ƙafafunta na gaza ɗaukanta. Tafiya take amma gani take kamar sawayenta basa tafiyarsu yadda ya kamata, hakan ne ya sanyata fara tafiya da sassarfa hannuwansa ya buɗe mata kai tsaye ta faɗa jikinsa tana fashewa da kukan data gaza yin irinsa. Ɗumin jikin pappanta na ratsa nata jikin pamp na bayanta ya shiga shima hawayen na wanke fuskan shi. "Mabuɗin ko wacce iriyar nasara shine haƙuri da ƙoƙari da sadaukarwa Umami! Allah ya biyaki ladan bautarki ubangiji ya sake haskaki keda zuriyarki kufi haka Alhamdulillah ba abinda. zamuce da Allah se godiya ba loƙacin kuka bane wannan umamin Khairi loƙacine na farin ciki muje ga sauran ƴan uwa" Yay maganar yana kama tafin hannunta ya sumbata tare da furta "Allah ya jiƙan khairi ya kai haske ƙabarinta!" ya faɗi muryansa na rawa da raunata sosae. Kuka ta saki sosae tana ambatar "Amin amin ameeeen ya habibullah!" taku ɗaya yayi ana biyu idonsa suka sauka akan Anne da Razeenerh dake rike da hannun Meerah ɗayan kuma riƙe da hannun Annen sun sanya zeenerh a tsaƙiyarsu. "Ya Allah!" Ya furta wani abu na sake bin jikinsa gaba ɗaya yana tsirga masa, zame hannuwanta tayi ana Zeenerh'n Anne tayi ta fara tafiya itama da slow slow tana jin kamar bata tafiya, tana zuwa ta rungumeshi gaba ɗaya kuka na kwace mata. Mutumin da kullum seta saurari ƙira'arsa ko ƙiran sallarsa ashe shiɗin kakantane? Lallai ikon Allah baga taɓa karewa muryansa ce ta dawo da ita daga duniyar tunanin data faɗa. "EASHERH ASH (DIDI) barka da sake wanzuwarki a cikin tsatsaon Ash da Aliyullah a karo na biyu KHAIRIE'N ANOUR!" ya faɗi kasancewar shi da kansa ya mata huɗuba har cikin masarautar EMAAR's. "Pap!" ta faɗi tana sake ƙankameshi. "Ashhh zata karasa ɓalle muku tsoho fa umami!" Sheikh Aliyullah ya faɗi da murmushi a zuciyarsa. Nuni yay da meerah akan tazo "Kodan ita ƴar ƙauyece renon wajen ƙasa shi yasa bata magana" ya fadi yana kama hannunta daidai ta iso. "Ni kaina ba nace ka sadda naga yarinyar nan tayi magana ba Habibullah!" Queen lajja ta faɗi da wasan nan irin na jika. "Allah nidai ina magana Pap!" Ta faɗi da sunan da taji Annenta ta faɗi. "Shi yasa da Allah ya tashi haɗa aurenta seya haɗata dame irin halinta sakk wancan wani me murɗadɗen halin jikan naka" Wannan karon jedderh ce tayi maganar da murmushi a fuskarta. "Oh ohhh! Ba'a shiga tsakanina da *ABDOUL-MALEEK* umami don zan iya cewa tun kafin ki sanshi na sanshi. Zan iya rantse miki cewar namafi iyayensa sanin halinsa ciki da bay ko Ayaanan?" ya fadi yana kallon Ak ɗin daya ɗauke kansa. Wata katuwar harara Ak ya jefama tsohon yana hucewa fuuuuuu ta gabansa. "Ummmmm nayi lefi kenan?" tsohon ga furta yana shafa sumar kan Alhassan daya iso gare shi bayan ya zame naɗin kansa. "Da dukkan alamu kan umami ya sami taɓi kaɗan kinga hasalin jikan anan!" ya faɗi yana nuna mata mahaifi ga Ak wato Sarki Hassan Al-hassan ashaan. "Se a hankali abubuwan zasu ƙarasa daidaita Sheik" kai tsaye Alhassan emaar's ya fadi.daga nan suka fara shishshiga cikin manyan motocin da suka zo ɗan ɗaukansu. Sheikh Aliyullah da Alhassan a gaba se lajja da jedderh a baya. Anne,Razeenerh, motarsu daban suna baya Raiha jikin anne da duk take a takure kasancewarta mutum bame son yawan shiga mutane ba, se adeenerh a gaba. Se ya rage meerah ce kaɗai bata samu abokin hadi ba kuma tana tsaye ran nan fall don yau kam ƴan zuciyar sun motsa ba laifi. Tuni idanuwanta suka ciko da kwallar takaicinsu harda ma Annen data shigewarta ta barta. "Karki ɓaga min fuskanki da ruwan hawayen da suka kasance masu daraja a gareni *✯MIFRAH♡* taji muryansa ta bayanta ya daketa tare da ratsa har cikin jikinta. se kuma jikinta ya dan fara rawa ta cira ƙafanta ta fara tafiya da niyar barin wurin taku ɗaya ana biyu taji sauƙar tattausan tafin hannunsa cikin nata tafin. Ta bayanta ya ɗoro kansa saman wuyanta ƙamshinta ya shaƙa kaɗan tare da lumshe idanunsa cikin muryan daya tafi kasa can sosae kamar me yin raɗa ya furta. "I will miss u *✯MEEFRAH♡!!!*" ƙoƙarin zamewa take ya sake janyota cikin jikinsa yana mannata da jikinsa "Uyummmm ke bakiy kewana bane?" ya sake jefa mata tambayar yana sake cusa kansa cikin wuyanta da yake shaƙar ƙamshinta sosae. "Sa ke ni kaga duk kowa ya tafi ya barmu amma ko!" "Har abada ba zan taɓa sakin kiba baby!" Ak ya faɗi yana ɗaukarta cilak ya nufi wata bugaggiyar black car da ita kaɗai ce ta saura. A kujerar kusa da driver ya ajjata ya zagaya shima yana komawa mazaunin driver. Shi da kansa ya taka motar yana yin wani kalan Reverse kana ya ɗauki wata hanya ta daban ba wacce taga sauran motocin sun ɗauka ba. Ɗan ɗago kanta tayi idanu ta har na cikowa da ruwan hawayen da suka tara murya na rawa ta furta "Ya naga mu ba irin hanyar da suka bi zamu bi ba?" lips nashi yaɗan lasa kaɗan tare da faɗin "Kema zakije amma kafin nan se kinyi woni aikin lada" idanunta ta zaro kaɗan tare da faɗin "Aikin lada kuma wanne iri?" Be saki hannunta dake cikin nashi ba ya furta "zaki gani ay!" Daga haka yaci gaba da tafiya ai kuwa ta sakar masa kuka tana ihu tana faɗin wllh babu inda zai kaita don dalilin ya saceta ma. Murmushi kawai yay wanda ba kasa fai ya fiya yin irin saba sakalcinta tsoronta da ban tsoronta shineabu na farko daya fara rinjayarsa akanta. Lips nashi ya ɗan ciza kaɗan bada yawa ba tuno Nigeria dayay da loƙacin data fara zuwar masa cikin tunaninsa da baccinsa. Kuka sosae take taƙi yin shiru dole ya karkata tafiyar da yay niyar yi da ita don harta fara bashi ciwon kai kaɗan, a katon get ɗin katafaren gidan Sheikh Aliyullah Dawood ya perker car nashi cikin get na biyu wanda shine na karshe. Tunda suka shiga gidan take binsa da kallo don yanayin ciff ɗin gitan ba ƙatamin burgeta sosea yayi ba. Don ita indai za'abi zaɓinta batason ire iren waɗan nan mahaukatan gidan masu shegen girma da haɗa tarkace da yawa burinta gida irin wannan shima za'a ƙirashi da ƙarami ba haka ba za'a ƙirashi da babba ba. Motocinne kusan sha biyu jere a compound na gidan, ga hasken streetlight ya zagaye ko ina na gidan a dede bakin duka mahaɗara babban palon gidan ya parker shi da kansa ya fita ya bude masa kasancewar dama su mazajen larabawa tamkar bayi suke akan matayensu komai su suke ma mutum hatta goyon yara namiji zaki gani da irin jakar nan ta ƴan gayu lol😁 rataye a wuyansu da babyn ciki. Hannunta ya kama suka shiga a tare baki ɗaya palon ya kacame da tarin hayaniyar jama'ar da dammm suka cika palon. Suna shiga Asha Anum ta taho da gudu tana rungume Meerah da sakkk basa da woni banbanchi sena hasken fata kawai itama kuma ba sosae ba kasancewar a yanxun nata fatar itama a murje yake ba kamar baya ba. "Wllh kawai Maama na da Annenki a twins suka haifomu se akai mantuwa kowa mamanshi daban da babanshi" ta faɗi tana sakin dariya abunta. "Asha Anum kammmm..... Pappinta ya faɗi kamar zeyi kuka dama ga hayaniyar nan na ƙokarin fasa kanshi kasancewarshi mutum bame son hayaniya ba. "Da gaske nake ko Mammiy?" tayi maganar da kallon mahaifiyarta murmushi kawai Oum anum asha tayi tana jinjina har yanzu Asha ba zata nutsu ba kenan. Abinda aka riga aka so niyar aikata mata bazai taɓa barin ƙwaƙwalwanta ya huta ba. Cike da tausayinta ta gyaɗa mata kai don ganin abinda take tamkar wanda ciwonta da kamat name iska ne ke neman tashi. A duniya babu abinda yakai cutar razanin kwaƙwalwa ban tausayi barin ma ace da yaronka lafiyansa kalau sama taka ya gamu da hakan. Zama tai taƙi kuma sakin Meerah ɗin kan Queen teemah'n Alieyo ta kusan faɗawa da sauri Alieyo ya mike zaram yana faɗin, "Asha ki kula man!" Ya faɗi a dan kausashe don ganin suna koƙarin danne may Jaan ɗinsa. Gaba ɗaya palon dariya suka saki don duk babu wanda besan halin Alieyon ba akan sunshine nashi wanda yake jinta tamkar tafi ma rayuwarshi. Bakinta ta murguɗa may tare da hararan Queen teemah. Kwafa teemah taja tana ɗauke kanta don wasu na tsokanarta cewa tunda mijinta yaƙi auren Anum babba don haka zasu bashi anum asha karama seya aure. Duk da kasancewar ta fara manyanta kaɗan amma se duk take jin haushin familyn dangin Ammien ma duka. "Wai ina ƴar Al'ajabi take ne liey Anum babba ta tayi tambayar da gayya don kawai ta fusata Queen ɗin. "Tana gidan mijin ta mana ko kin zata itama se tayi kwantai irinki kana tayi auren to tana can England tare da mijinta uhummmm" ta fadi tare da hararar Anum babba. Haba wa me za'ayi inba dariya ba harshi kanshi Alieyon dariya yake mata. Jin an anbaci Alieyo da kuma queen teemah da sunshine da jaan da taji wasu mutanen ke ambatane ya sanya meerah saurin kallon queen. Itama kallonta tayi se kuma ta miƙa mata hannun alamun tazo, bayan ta zaunar da meerah kusanta ne meerah ta dan saci kallon Qeuun ɗin kaɗan. Cikin muryan kasa sosae tace "Auntiniey!, don Allah in tambayeki?" murmushi queen tayi tana fadin "Tambayeni mana Allah yasa na sani" "Insha Allah kin sani" "To ina jinki" ta fadi tana komar da nutsuwarnta kaco kammm kan meerah "Amm dama don Allah ko kece wannan ta cikin labarin Littafin AMMEYLAYLERH na KAUNA BIYU?, amma don allah kar kiga kamar ko na rena miki hankali ne, tunda tace wasu abubuwan sun faru da gaske kuma da gaske ita kanta ta cikin labarin suna da alaƙa da ita kuma ma tana nan tana rayuwa a duniya matar kuma har masoyinta na farko *ALIYU SHUREIM* daya rasu duk a gaskiya ne da Haihuwarta na farko da tayi na ban Al-ajabi!" Hannunta da yaƙe cikin na meerah ɗin ta jimƙe a nata jikinta na ɗaukar ɗumi kafin wani ruwan kwalla ya cika mata idonta amma tayi saurin sanya kifa tafin hannunta tana sharewa. "Kwarai ni ce! Ni dai kaina na bata kaɗan daga cikin labarin nace ta rubuta da yarjewana dana Mijina ma" sake riƙe hannun queen meerah tayi cikin ƙasa da murya sosae don kar a fuskanci akan maganar da suke ta furta. "Allah ya jiƙan Aliyu shureim" "Ami amin ameeeen ngd" ta faɗi muryanta na rawa kamar zatay kuka sedai alƙawarinta ba zata sake zubarm da shureim ɗinta hawaye ba. "Shine nima nake son bata *LABARINMU* ta rubutu amma kuma ina jin kunyanta kuma kar naje ko zata disgani ko tace ba zata rubuta ba! a yanzu haka ina gaisawa da ita sama sama" "Ba komai ba haka take ba ita wllh nima da farko nasha zan samu wannan dan garɗar sedai wllh ba haka take ba idan kina jin *TA DABAN* to wannan itace wllh duka Fan's nata zakiji da fatan alkahiri da gama da duniya lafiya suke binta. Idan kuwa suka jita shiru a duniyar online sun ringa ƙiranta kenan kuma ita bata da shamaki da ƙira daga Fan's nata don Sim card na daban ta ware musu samm bata da wulaƙanci ire iren na wasu ɗaiɗaikun mutanen da dan sunga sun fara zama wani abu shikenan se zarra da girman kai su tashi a yanzu haka in kinji yadda take wasa da dariya da fam nata abin seya baki mamaki. A yanzu haka ina cikin wani group nata amma bana magana sosae SUNAN GROUP ɗin *SPECIAL* _{Ta Daban_} wani novels da zata fara da wata Actress (Ƴar wasan hausa) ta bata labarin rayuwarta tace ta rubuta mata" Wata ajiyar zuciya meerah ta sauke tana gyara zamanta tare da kuma da faɗin. "Tabbas naga hakan nima Auntiniey Insha allahu kuwa nima zan bata namu labarin rayuwar ta rubutu don ganar da al'umma cewa duk inda ɗan adam yake ba abin wulaƙantawa bane. Kuma dama shi haka lamarin duniya yake abinda ya baka dariya wata rana ze juye ya baka kuka. Haka abinda ma'ana ɗan haƙin da aka raina shike tsole idon maƙiyansa." "kinyi tunani me kyau kema Meeran Anne au ko nace ta AK!" Hannuwanta ta sa tana rufe fuskarta tare da fadin "Allah ni ba tashi bace ta annen dai" Wata kafurar harara Queen ta sakar mata tare da faɗin "seki zauna sokanci da sakalci yanda suke kewaye da dangin nan nasu a liƙa mishi wata" wata kalan zaro ido meerah tayi tare da faɗin "Iyeeeeeee! Na'am!!!" ta ƙarfin daya dawo da hankalin kowa kansu. Idonta be sauƙa kan kowa ba se ana AK da dama tuni idonsa yake kanta. Baki ta murguɗa masa tana ɗauke kanta. "Ba dai kyau munai munai uhum donma mutum yaji" Anum asha ta faɗi tana murguɗa musu baki, rankwashi Queen ta kai mata taui saurin zamewa tana mata gwalo. Daga nan kuma aka saɓunta gaisuwa aka sake gabatar ma da juna kai nan masu kuka sukayi masu tausayi ma sukayi ƙiran sallar magrib da akay ne ya sanya mazansu miƙewa suna fita baƙi ɗayansu cike da burgewa daga nan suma matan suka mimmike masu yin. sallar nayi masarayi kuma suna dasa sabuwar fira. ★ Se bahan sallar isha'i kana mazan suka dawo na cikin makkan na tafiya gidajensu masu kwana kuma kowa na kama abokin kwanansa, Queen ce ta miƙe da sauri meerah ta miƙe itama tana bin bayanta. Se daga baya queen ta lura da duk inda tayi nan meerah ke yi, tsayawa tayi tare da tambayarta ko wani take nema amma setace mata a wai ita zatabi ita a wurinta zata kwana, wata ƴar ƙaramar dariya queen tayi tare da kama hannun meerah tana juyota gabanta. "Idan kika bini ni kuma nayi ya da nawa mijin?" "Don allah auntiniey naga kowa wanda ya sani yake bi ne ni kuma ke kawai na sani ita kuma anne ganin ƴan uwanta ya sanya ta manta dani ne ma fa pls zan biki nikam kawai" Haba queen ta riƙe tare da furta "Wa rabani wllh ba zaki bini ba nima wurin nawa mijin na nufa kema kibi naki ai kunfi kusa a yanzu baki da makusancin daya fishi a cikin wannan duniyar! Don haka nemarshi wllh ba zaki bini ba ahammm" Saƙeƙe meerah ke bin queen da kallo tana kallonta kuwa tayi gaba ta shige motar mijinta dake ta mata hong tun ɗazun. Ji tai an ɗan rungumota ta baya jikinta na ɗan rawa tayi saurin juyowa tar idanunta suka faɗa cikin nashi. kansa ya kwantar a gefin wuyanta tare da faɗin "Kinga yadda ake ririta miji ko? Idan kuma baki so ne kawai se naba wata dama a family a ɗaura kinga dama gobe juma'atu ce babbar rana sena samu tabarrakinta kenan" Ya faɗi yana ƙashe mata ido ɗaya. Ture kanshi tayi cikin wani fushin da taji na taso mata ta soma tafiya da sauri¹. "uhmmmmmm Ashe dai ana sona baƙin cikin nuna min kawai ake" ya faɗi cike da muryan zolaya amma samm bata gane zolayartan yake ba a fusace ta juyo tare da faɗin. "Allah ya kiyashe ni naso ka never forever wllh kaje ma a ɗaura maka da mata ɗari" Ta fadi tana juyawa fuuuuuu. Cilak yacira abarsa yana nufar danƙareriyar blue black ɗin ɗaya daga cikin jerin car's ɗin dake compound na gidan. Shure¹ take famar yi tana son taga ta kwace amma ta gaza kamar ɗazu seda ya zaunar da ita kana yaja motar suna barin gidan gaba ɗaya. A wani ƙayataccen madaidaicin gida ya paka sake ɗaukarta cilak ya sake ɗaukarta yana yin cikin ainihin gidan da ita. Zaunar yay akan sofar dake gaban bed ɗin bedroom ɗin yana shigewa bothroom, shure shurenta taci gaba dayi tana ƙananun kukanta tana a yadda ya barta harya fito ɗaure da fari tass ɗin towel me laushi da taushin tsiya tsarbar farin har wani hasken blue kaɗan yake bayarwa. Webdroop ɗin dake shaƙe da kayayyaki na mata dana maza ya nufa wasu tausasan riga da wando marasa hannu ya ɗebo tare da komawa gaban mirrow'n ɗakin. Duk abinda yake ta ƙasan idonta take kallonshi sebin farar fatar jikinsa data haɗu da hutu da jin daɗi take wacce take wani shaning da ɗaukar idanu game kallonta. "Malama ki fito kai tsaye ki kalla mijinki ki dena woni ɓoye ɓoye da sinne kai kamar wata ta gari" ya faɗi yana zama akan stool ɗin mirrow'n lotions masu tsada da tausasa fata ya shiga murzawa a saman lafiyayyar fatarsa. "Oya tashi kije ki wo wanka don tsarina bana bacci kusa da wanda yake tsamin dauɗa" "Bazan yiba idan kuma zaka min se naga!" ta faɗi tana mjrguɗa masa da micilon bakinta me kama da gidan tsutsa. A natsensa yaci gaba da shafa mansa tare da sauran uzirirrikansa, babu tsammani kawai taji yayi sama da ita idanu ta zaro woje cikin muryan in inar data rasa inda ta gada ta furta. "I...Ina ku.....ku...ma....za..ka. ..kaini?" "Ba abinda kika buƙata kenan ba zan miki wonkan ne" ya faɗi kai tsaye cikin muryan nan ta no nonsess. Dukan ƙirshin da be gama ɓalle maɓallan gaban rigar ba ta shiga yi tana me faɗin "Ni wllh sheerri kamin Allah ba ce nay kamin wonka ba, da girman nawa zance kamin woni wonka dan mugunta kodan kawai kaci zalina!" tayi maganar tana saken ijiyar zuciya. Taku yake yana sake kusantar bedroom ɗin beko saurareta ba bare jin maganganun da take faɗi ɗin. Seda ya dire da bathroom ɗin kana ya shiga kiciniyar cire mata top ɗin dake saman riga da wandon dake jikinta na palazzo robe. Kuka ta sanya mishi tana faɗi. "Ka fi ta! Ni zan iya! Bana so bana so! Wllh bana so" ƙyaleta yay yana faɗin ya bata nan da 30 mints tayi sauri ta fito. Kai tsaye car key na motan ya ɗauka yana fita cikin abinda bai wuce 15 mins ba se gashi ya dawo hannunsa riƙe da ledoji manya guda biyu. Befi ten min da zama se gata ta fito kamar ranar jikinta duka nannaɗe da fararen towel tamkar wota fatalwa. A wannan karon kam seda sautin murmushin daya saka ya fita don ya gaza ɓoyuwane. Cikin danne dariyar kuma dake son kubce mishi ya furta "Koma ki ɗaura alwula malama" ko inda yake bata kalla bare yayi tunanin zata tanka shi. Tsaye ya miƙe tsammm yana nufar ind take ganin yayo kanta gadan gadan ne ya sanya ta zurawa zuwa cikin wedroop tana faɗin "wllh da Alwulana na dauro ma tsaya kaji" Wani lalataccen murmushi yay yana komawa zaune. Sauri sauri take birkitar wedroop ɗin cikin wannan muryan nashi ya furta. "Kin neman wani abune?" "Um-um na ganshi ma" Ta faɗi tana sake cusa hannunta don samun wasu kayan, ganin bata samu bane ya sanyata ƙoƙarin maida waɗan da ta cire. Ganin tana ƙoƙarin maida kayan data cire ne ya sanya shi dakatar da ita wasu riga da wando masu tsayi da santsi ya bata yace ta saka. Ganin kayan da mutuncin sune ya sanyata yarda tana amsa baya ta juya masa wandon ta fara zirawa kana ta zira rigar da yadda bata yarda yaga wani shashi na jikinta ba. Himar ya bata wanda yazo mata har ƙasa kan dardumar dake kallon alkibla ya nufa yana mata nuni data biyosa. Sallah yajasu raka'a biyu bayan sun idar ya dafa saman goshinta tare da karanto adda'ar sa annabi ya koyar a daren auren ma'aurata. Dake wancan karon yana ba'a hayyacinsa bane ya sanya hakan bata samu ba se a wannan karon. *"_Allahumma inni as'a luka min khairiha wa khari ma jabaltuha alaihi. Wa Auzubika min sharriha wa sharrima jabaltuha alaihi!" Daga nan se sauran adda'oi suka biyo baya nan ya shiga jera mata tambayoyi kamar yadda koyar annabi take. Duka tana bashi amsar tambayoyinsa be sameta da ɗangarta ba ko ɗaya daga inda suke ya miƙa hannuwansa gasassun naman ɗawisun daya shigo dasu yanzu da zafinsu ya buɗw musu. Turirin ƙamshi da daɗinsu suka bugi hancin meerah haba sega meerah ɗinmu da haɗiyar wani mugun yawu lol. Kamar yadda nima ina daga nan na haɗiyi nawa lol banda dariya. Da kanshi ya shiga ciyar da ita babu fulaƙon komai meerah ɗinmu ta zage ta dautsi naman ɗawisunta lol tana korawa da zazzafar madarar da su dama basa rabo da ita koda yaushe. Ƴar ƙaramar gyatsatayi tare dayin hamdala tana miƙewa tsaye ta koma saman sofa abinta tana kobciya abinta. Seda ya kammala kana ya kawar dasu daga wurim yana medasu cikin fridge ɗin dake daf da ƙoyar fita. Brush yayo kamar yadda itama seda tayi kana ta konta ɗin, saman lafiyayyen gadon dake tsume cikin wani farin tattausan farin duvet da ya sirka blue. "*✯MEEFRAH♡!!!*" Ya ƙira sunan a wani irin nutse "Na'am" ta amsa shi. "Dawo nan" ya faɗi cikin muryan bada umarni yana ɗauke duka fara'an kan fuskanshi. Fuskanta ta yamutsa tare da faɗin. "Ni wllh kamar kan sofa zan kwana" tace tana me sake gyara kwanciyarta da kyau. "Ok zata ishemu ai" yana saƙkowa a gadon. {Na shiga uku} ta furta tana zaro ido irin na marasa gaskiyar nan. Ko kafin tayi wani yunƙuri harya iso kan sofar yana shigewa cikin jikinta. Saurin tashi zaune nayi ina kakkare ƙirjkna da hannuwana sejin sauƙar hanniwansa nayi kan nawan yana zame nawa hannun tare da mayewa da nashi soft hannuwan masu azabar laushi kamar na jinjirin da aka haifa yau.. Wani kalan riƙo hannuunsa nayi idona kamar zasu faɗo kasa. Cikin wata matacciyar murya ya furta "Sleep tight baby" Ya faɗi yana kwantar da kaina saman ƙirjinsa. "Ni sanyi ma nake ji" nai maganar duk don son na kubuta. "Ohh!" ya furta cupping fuskanta yayi da hannunshi, hakan yasa meerah zuba mashi idanu itama tana kallonshi. Kasa ci gaba da kallonshi tayi tana sadda kanta kasa not saying anything saidan ita kaɗai tasan irin halin da zuciyarta yake ciki na tsananin bugun da yake mata wanda ta tabbar na tsoro ne. Ahankali yakai lips nashi saman nata yana zaro harshensa dake ƙamshin mouth wash ya ɗora saman tattausan lips nafa ya ɗan lashesu tight cikin nutsuwa da sanyi , lumshe idanunsa yayi tsananin feelings ɗinsa na ƙaruwa akanta. Saiya ɗago fuskanta gaba ɗaya ta yadda zai kalleta da kyau, yana nutsa duka hannayensa cikin lallausan gashinta tare da zubama red lips nata narkakkun idanunsa. Yanda ya sake lasan lips ɗinta ne ya sanyata jikinta fara ƙokarin rawa.sake shigar da ita jikinsa yayi da kyau yanajin ƙirjinta da babu komai na neman ƙarasa kashe sa da ransa tare da ƙarasa konce masa notikan kai. Ƙanƙameta yayi jin komai nashi na ƙarasa koncewa fuskansu ya hade wuri guda wanda hakan ya tilasta mata buɗe idaunuya. Ba ƙaramin firgita tai ba da ganin yadda kwayoyin idanunsa suka sanja launi tamkar woni bugagge. Mjryansa a shaƙe matuƙa tamkar irin wanda ya shawu sosai ɗin ya furta. "I need mifrah nd I love u baby!!!" Yay maganar da in ina jikinsa na wani irin tsumar dashi kaɗai yake jinsa haka jikinsa don matsanancin feelings. Anan kan sofar komai ya faru tun ina tunanin zafi da ciwon da zanji se naji saɓanin hakan yau. Don sammm ba irin dararen ranakun ranan bane. This kiss is not pie pierce but gently, there is no anger in it no sadness. Just love lots and lots of love amma kuma. Just like no dararaen ranakun baha it took away all my sense. Bayan komai ya lafa idanuna a lumshe ina cikin jikinsa a kwance luff se shaƙar wannan dadɗan unique ƙamshin san nake. Ni kaɗai nashiga tunani. Anya akwai namiji irin *YAYA KUWAIT AK* kuwa? Don shi irin mazan nan ne The Man that guy is fire in bed. A hankali taɗan cizan lips nata tana sake cusa kanta cikin ƙirjinsa da babu riga tana sake lafewa luff tamkar wota ƴar mage. Ahankali wannan abin me kama da ƙaunarsa taji kamar yana sake mata dabai baiyi a cikin duniyarta, {I LOBE U muah}. ta faɗi can kasan zuciyarta. Jitay yaja ijiyar zuciya tare da furta "And I will lov u for everything mifrah!" "ni bance komai ba ai" ta faɗi tana sake kanainayeshi da duka hannuwanta. Daga nan wani kalan daddan bacci yay awon gaba da ita a cikin jikinsa tana ji wannan abin na sake baybayeta. Washe gari juma'a be mayarda ita ba duk da ƙorafin data ringa may. Haka suka ƙara kwana abinsu suka sha ƙaunarsu. Har zuwa wata washegarin daya kama asabar kuma a ranar ne zasu wuce madina. Farkawanta kenan daga baccin daya ɗan fisgeta A hankali ta shiga ware lumsassun idanunta, sai kuma tayi saurin komar dasu da sauri ganinsa babu riga a jikinsa se wani short ɗin guntun wando. Har yanzu ta kasa sabawa da ganinsa haka babu kayan arziƙi jikinsa tana matsawa can ƙarshen gadon. A hankali yasa kafaɗarshi ya maƙale wayar da yakeyi kana a hankali ya matsota jikinsa kana cikin nitsuwa ya ɗan kalleta kana a hankali ya furta. "Irin idon xena warrior princess gareki ✯MEEFRAH♡!!! yadda kike sarrafasu kuma tamkar yadda Deepika pedakune ke saffafa nata. I love your gold eyes" Ya faɗi in sandly voice yana shigar da ita cikin ainihin jikinsa da babu riga...... *BY AMMEYLAYLERH* Hhhhhhhhhhh Mu kwana ƙalau na tahinku bacci nimaaaaa😬😦 *🦅 MIKIYA 🦅* _A wonderful world & Special anti terroRism squad_ ____________________ *MARYAM NASEER MIRRAH* ~AMMEY LAYLERH ✍️~ ✯ *~🌠 JAJIRTATTU WRITER'S ASS.... 💫~* BOOK Two…………………………񆬍✍ # Hot Romance scene # Real life # Hot love scene # Ak meerah # A.k.a AMMEYLAYLERH👍👉 *Bɪꜱᴍɪʟʟᴀʜɪʀ Rᴀʜᴍᴀɴɪʀ Rᴀʜɪᴍ* ♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡ ★ 35&36 "Ehhhhhh lallai wuyanka ya isa yanka DUD! wato da ace bani da mata tuzuru ne ni kamar *TAJ EL-MUAZ AFIF* ɗin *AMEESHERH* {na cikin littafin *AMMEYLAYLERH* me suna *SPECIAL* {_Ta Daban_ } Kenan da seka haukatani ko me kake nufi? Tunda har zaka amsa woyana kana a irin wannan yanayin ɗan iska kawai" Daga can ɓangaren me wayar *MALEEK TOUFIQ* ya katse shi yana runguma *Ashnour* tashi jikinsa shima. Ɗan zame woyar Ak yay don wllh shi yama manta cewar woya yake yi da Maleek toufiq ɗin shima dai ɗaya daga cikin littatafan *AMMEYLAYLERH* Ne me suna *KAREN BANA* (maganin zoman bana). Datse woyar yayi yana jan ƴar ƙaramar tsuka tare da birkitota jikinsa tana komawa kan ƙafafunsa. Ganin ya kafe wuri guda da kallo ne ya sanyata kallar inda yake kallar saurin jan armless ɗin dake jikinta sama tayi. Tare da ɓata face nata tana ƙoƙarin sauƙa daga jikinsa. A nutse cikin sanyi da nutsuwa ya sanya hannuwansa yana zagayo ƙugunta dashi, ɗaya kuma ya saƙalo wuyanta yana matso da fuskanta dap da nashi. Ƙamshinta ya sake shaƙa Yana buɗe Idanuwansa da suke bayyanarda abinda yake ji a zuciyarsa akanta. Hannunsa ya saka ya juyo da ita yana kallan kyakkyawar fuskanta data kasa ɗagowa ta kallesa saboda yanda take Jin kirjinta na bugawa na tsoron ta buɗe ido ta kalli abinda ze kusa tafiya da numfashinta. Wani kalan lasan fatar wuyanta yayi wanda hakan ya tilastata buɗe idanunta da suka tara ruwa suke gaf da zuba.Idanuwantan dayake jiran ta ɗago ya kalla ta buɗe akansa, yarrr ya wani ji tsikar jikinsa sun tashi wani mayen feeling nata na neman fasa kansa. Kallon cikin ƙwayar idanunta kaɗai kasheshi hakan yake yi. kallan da ya sakar masa wani mayen feeling ɗinta sabo, sake lasan fatar wuyanta yay still. Wani kallo ta jefi fuskansa dashi wanda ya sanya idanunsa yin luuuuuu tamkar wanda ze some mata. wata fitinanniyar ajiyan zuciya ya sauƙe tare da rintse ido ya buɗe yana sake shigar da ita jikinsa ya rungumeta gabaki ɗayanta ahankali yana jin zuciyarsa kaman zata fashe akan mayen abinda ke ɗibansa gareta. Ruwan da suka cika idanunta suka sanya mata ƙyallin idon ne ya gangaro ta gefin kwarmin idonta.cupping fuskanta yayi tareda matseta jikinsa ahankali Cikin nutsuwa yakai bakinsa kan kunnenta da wata lafiyayyan murya me wani irin sautin daya sakata rintse Idanuwanta da ƙarfi tana ƙanƙameshi. "Kinsan illan da wanɗan idanun suke haifar min kuwa?, kin san tun yashe waɗan nan launin idaniyar suke illata rayuwana *MEEFRAH!* ?" ya faɗi yana kasa ci gaba da kissing nata yay ya saketa a hankali yana ƙin kallan Idanuwan, saboda ka kashesan da Idanuwan keyi. Kan lips nata ya ɗora bakinsa yana ɗan jujjuya nashi ahankali tare da gangaro da hannuwansa saman wuyanta yana ɗan shafarsa kaɗan. Sake mutuwa jikinta yayi kanta ya tsaya daga tinanin komai bayan rintse Idanuwanta datai tanajin yanda bakinsu yake haɗe har loƙacin yana kissing ɗinta cikin wani irin sanyi da fitinannen yanayin dayake sake rikitar da tinaninta. wuyanta yayi ma wata shegiyan shafa yana maida bakinsa wuyan ya ɗora lips nashi yay wani kalan kissing ɗinsa yana gangaro da kansa kan kirjinta dayake kalla kafin ya buɗe gaban rigar ahankali fatar kirjinta da mu nigeria kai tsaye da fara zamu ƙirata saidai su acan kai tsaye chocolate colour zasu ƙirata wanda tsananin hutu da hutu da lafiya ta fara bayyana tare da murjewa yabi da wani kalan shegen kallo. Kansa da duka sassan jikinsa na neman zarewa wajen gaza countrol na kasa sarrafa kansa. Wani numfashi me ɗumi ya fesar yana kife kansa akan tsakiyan ƙirjinta. Yana zagayeta da duka hannuwansa yana ƙoƙarin sarrafa numfashin da yake son se yabar jikinsa. ɗago hannuwanta da ƙyar tayi tana ɗorawa akan hannuwansada taji suna rawa batare data iya ɗagowa ta kalli cikin idanuwansa ba. Itama nata jikin na dan soma samin ɗumi. Lallausan tafin hannunsa ya sanya ya zare nata yana zuba mata Fitinannun idanunsa da suke a janye ya ware a kanta cikin wani irin mayataccen salo yay kissing eyelashesh nata. ƙara narkewa a jikin sa tayi abinda takeji akansa ita na wujijjiga tunaninta, Shanyayyun Idanunta ta zuba masa tana ma rasa me yakamat ta fara masa. Se kawai ta wasu ruwan hawaye masu ɗumi suka shiga saƙƙo mata suna bin saman fuskanta. Wani irin shigar da ita yayi cikin jikinsa tare da ɗora bakinsa kan idanunta yana bi yana lashe ruwan hawayenda duk ya zubo mata tare da ware tsumammun idanunsa a kanta yana kallon tsananin tarin ƙaunarsa a cikin tsaƙiyar ƙwayar idanunta da babu ƙarya. Kallon da yake mata ne ta kasa jure masa saboda tsumata da idanun nasa keyi da wani irin yanayi me wahalar fassaruwa. Shi ɗin ma itan yake kalla ganin kallon da takeyi masa ne yasa shi ɗan lumshe idanunsa tare da buɗesu aloƙaci guda, wani kasalallen wutar abinda yakeji akanta na sake lunkuwa akanta. Sunanta ya ƙira akasalance, Idanun da ruwan hawayen ke zuba ta sake zuba masa tana me kallon chest ɗinsa dake a bayyane se kuma tayi ƙoƙarin haɗe yawun daya tsayar mata a maƙoshinta abu biyu na tsirgar mata tsoransa da kuma abinda take ji akansa saboda ganin sa da tayi babu riga ya sanya ta jin tsananin feelings nashi ga kuma tsoro. Idanunta ta rumtse tare da ɗora bakinta saman chest ɗin nashi tana sakar masa wani fitinannen sumba. Wani irin jan numfashi yayi tare da fitar da wani sauti gami da zuro tongue ɗinsa ahankali ya lashi lips ɗinsa domin sosae kiss ɗin ya shige shi. Wani kalan runguma ya mata tare da soma birgita tunaninta, domin wasu irin zafafan abubuwa ya shiga aika mata masu wuyar fassaruwa, Romance nata yake idanu rufe sosae a abinda yake matan ya yamutsa kwakwalwarta. Daga haka fagen ya koma iyaka na masu yaƙin ƙasa da ƙasa. ★ Few minutes. Vebration na wayanshi shiya farkan dasu daga ɗan baccin daya ɗebesu bada jimawa. Ɗan cizan lips nashi yay wanda hakan ya zama kamar habit ɗinsa yana janwo woyar. Sunan Oum daya gani ne ya sanya shi karasa tashi zaune yana manna woyan da kunnensa. "Garga! Me kake yine wai da har yanzun baka kawota ba har sun tafi?" Wani ɗan numfashi ya fesar tare duban agogon dake bedside kana ya furta. "Oumm!" a ɗan shogoɓe yana matse hannun meerah dake cikin nasa kana ya furta "Zan kawota amma tomorrow!" "Umarni na baka ba shawara ba garga ayau duk dare nake son ka shigo madina okoy" Daga haka bata sake tsawaya saurarensa ba ta datse ƙiran, kyakykyawan farar fatarshin ya ɗan motsa alamar beso hakan ba. Gashi bacci take kuma beson ya tashe ta don haka ya ƙyaleta tayi barcinta duk loƙacin data farka sun tafin kawai, Sosae tayi bacci merai da lafiya. Tana farkawa ya ɗauketa wanka ya mata duk da ita bar yanzun ta kasa sabawa dashi don tsananin kunya hakan ke baya. Sedai kunsan mazan larabawa suba kunya garesu ba akan matayensu shi yasa komansu suke yinsa kai tsaye babu kunya babu komi gasu kuma da masifan son mata kamar tsiya, shi yasa suke zamewa matayensu tamkar bayi inda zasu sami abinda suke so suma bare kunsan san da masifan ƙaunar Black Niger. Bayan sun fito ya shirya ta shima ya shirya kansa ita dai se aikin sunne kai kasa take, daga nan seda ya jasu sallan Isha'i tunda dama loƙacinta yayi. kasancewar basu da matsalan komai a daren sukabi jirgin madina. Kafin su sauƙa har yayi woya an kawo masa car kasancewar inda yana tare da meerah bai son kowa ya jashi a motor, gaba ɗaya ko ina na jikinta a rufe yake dede ƙwayar idonta baka isa gani ba. A hankali wata babbar mota ƙirar Bugatti tylon gc tayi parking tsakiyar compound na masarautar, A natse ya ware gajiyayun fitinannun idanunsa hasken bulbs ɗin daya ɗauke idonsa ne ya sa yaja ya lumshe idon tare da ɗan taune jajayen laɓɓansa masu taushi kaɗan ba da yawa ba,wani zazzafan numfashi ya fesar ta bakinsa ganin yadda jerin perry mian suka zagaye motanshi. Cikin wancan ainihin harshensu juyayya suke jero kirari ga shi da meerah da take kwance kanta a damtsen hannunsa, Hankali kwance take kwasar baccinta rai fesss tun daga aiport ɗin kuwa. Cikin wannan kasaitar da izza ya ɗan zami kanta kaɗan gudun kada ta farka ya fita a motan. Da hannu ya musu nunin da suje kawai don bawai ƙaunar ihun nan nasu yake ba. Su kuwa da kallo suka bishi ganin shi kyakykyawa ajin farko da ko a cikin larabawan ma shi na daban ne. Dan se an tona kafin a sami kamarshi me kyau da kuma murjewan jiki. Allah ya bashi murɗaɗɗan jiki don kallo ɗaya zaka masa kasan cewa ehhh lallai tabbas shiɗin soldier ne,hannunsa yasa yana kare hasken bulbs ɗin da hanyar yanzu yakai ɗau akan fuskan shi da idonshi. Seda ya tabbatar sunyi nisa da barin wurin kana ya sanya hannuwansa yana mata ɗaukar baby. Cikin isa da taƙama haɗi da izza ya fara tafiya da ita jikinsa. Duk inda ya ya ratsa manyan perry mian ne da manyan bindiga fuskansu babu alamun rahama ga perry mian ɗin kiris kawai suke jira a basu umarni Mutum yayi mistake su mitsitstsike shi kamar kiyashi. Har cikin ainihin fadar masarautar ya shiga kasancewar masarautar ba baƙuwarsa bace. Duk kowa da kowa suna zaune kasancewar sunce se sunga biyunin asha amun data ringa fesama kowa cewar ga biyuninta can da Allah beyi uwa ɗaya uba ɗayane zasu haifesu ba lol😀 ba inji Ammeylaylerh inji asha anum ɗin lajja da pappi'nta. Suna daf da shiga palon da suke zazzaune ta farka ganinsu a wani wurin na daban ya sanya ta ƙarasa wartsakewa. Kan ƙafafunta ya direta duk da beso hakan ba amma ta shiga fisge fisgen daya sanya dole ya ajjeta kan ƙafanta, shine ya fara shiga da sallama a bakinsa amma can kasan maƙoshi ya yita. Tana bayansa se faman rakaɓewa take duk kunya kuma yabi ya dabay bayeta, da gudu asha ta janyota daga bayansa tana bayyana gaban dubban jama'ar palon. Zagayeta su kayi gaba ɗayansu kowa na rungumeta cike da tarin farin cikin cewar sun sami ƙaruwar har mutane uku loƙaci guda. Wato Anne, Meerah, Raiha.Cike da girmamawa ta shiga gaishesu amsata suka shiga yi sunata sanya mata albarka. Nan Ak ya gaysa da mazan ƙyal idonsa akan Maleek toufiq wata uwar harara maleek ya daso mishi. Dake gwanine wajen iya shariya sema ya ɗauke kansa tamkar be ganshi ba. Fitanshi yayi daga nan motanshi da yazo da ita ya buɗe yana ƙoƙarin shiga yaji an riƙo hannunsa ta baya. Jaalal Areef ya gani tsaye tare dasu maleek toufiq ɗin da kuma Alieyo, nan suka shiga masa iya shegen ya ɗauke yarinyan mutane ya gudu Hotel se yau ake ganin idonsa. "Duk ku ƙaraci iya shegenku duk nasan tarihin kowa ƴan banza har ƙara ƙara jalaal Areef tunda shi shiya nemi auren abarsa da kansa, ku kuwa fa wani harda yajin 7 months yama matar alhalin kuma yana sonta shegen girman kai da miskilancin tsiya ya sanya shi kasa saduda" yay maganar yana kallon Alieyo daya sha kunu tun kamin yakai kan Maleek toufiq ya furta "Kai kuma ai wannan ɗan shishshigin ne ya haɗa aurenka kamar yadda ya haɗa nawa besan dama sune zaɓin ranmu ba" mur AK yasha jin General maleek na shirin ɓallo masa ruwa gaban waɗan nan shegun masu shegen sanya idon tsiya. dake duk wurin aka haɗa kowansu seya maze suna sakin murmushin gefen baki daga nan kowa ya kama gabansa. Bayan yace musu sudai tsaya su gyara ƙasarsu don wllh saura ƙiris aikin daya kaishi yagama shima ya dawo ƙasarsa baki ɗaya. Kasancewar shi kansa jalaal Areef ɗin dss ne ya sanya suka shirya zama don dama duk iya aikinka woni ya dameka ya shanye kamar dai Ak. Daga nan wani ƙayataccen hotel ya nufa wanda yay booking nashi. ★Tsaye yake a gaban katafaren glass ɗin dake a ɗakin hotel ɗin da ya sauƙa, idonsa manne kan kyawawan gine-ginen dake garin. shi kansa garin yana masa kyau,yana kuma masa daɗi fiye da tunanin me tunani. Garin ma'aiki guda ai dole kaji yana burgeka musamman da daddare. Ƙaran wayarsa dake kan gado da ya ji ne ya sa shi waigawa. Sannan a hankali ya soma taku zuwa jikin gadon, ya kai hannunsa ya ɗauki wayar ganin oummun shine.da wani ɗan guntun murmushi a saman fuskarsa ya amsa woyar."Oummu mi yasa kike son koyan takura yaron kine ƴan kwana kin nan?" ya faɗi still murmushin bebar kan fuskan nashi ba jin abinda tace may. Ɗan faɗa fuska kaɗan yayi tare da farta "Naji" daga hakan woyan ya ƙare se wani motsa kyakykyawar farar fuskansa yake shi a dole an takura mai, tunda oum ɗin tace lallie yabaro ƙasar nan a gobe yabar meerah da ƴan uwanta su gana sosae. Aiki kaɗan yayi a systerm nashi kana ya kwanta yana ƙoƙarin ture tunanin meerah dake neman kutso kansa cikin rayuwarsa. Saidai ina duk yacce yaso yakice hakan amma hakan ya faskara kusan raba dare yay yana ta famar juye juye samen bed, yana tunano ɗumin jikinta, yanayin yadda take laɓewa jikinsa, yanayin shiru shirunta data koya wanda hakan sammm baya masa don yafi son kallonta a yanayin tsiwar nan nata.bacci ɓarawo gwanin iya sata koshi be samu damar iya satan Ak ba a wannan daren. Washe gari se wajajen sha biyi kana ya baro hotel ɗin, kai tsaye cikin masarauta ya nufa. Anne da Lajja sun riga sun fita wurin dangi irin tsoffin nan da suka musu saura, waɗan da basa iya fita ko ina seda su a samesu har inda suke. Amma meerah bata bisu ba don duk se take jin kanta a cikin cunkushewar yanayi. yana Sanye cikin wata sky blue ɗin long sleeve tees, sai blue ɗin wandon rigar. ƙafafunsa sanye da fararen sneakers Kansa sanye cikin pcarp., Se fuskansa kuma dake rufe cikin mask kasancewar besaba yawo haka sakaka ba ba tare da pcarp ɗin, bayan sun gama gaisawa da me martaba kai tsaye inda Ash ya faɗin masa meerah na can ya nufa. Kasancewan su hakan garesu ba komai bane. fitowanta daga bathroom kenan jikinta sanye da bathrobe fara ƙal ta ɗaure igiyoyin rigar saitin waist din ta, farar fatar da su suke ƙiranta da chocolate colour na ɗauke da damshin ruwan wankan da tayo, A hankali take tafiya tana tunkarar dressing Mirror'n ɗakin On stool chiar ta zauna fuskanta babu annuri haka babu walwala, tamkar bata da ƙoshin lafiya ne ko wani abunne ke damunta wanda yayi silar canzawanta haka. idanunta lumshe ta shiga shafa lotions ɗin Asha anum da suke cike da saman mirro'n Bayan gama shafa lotion ɗin feshe jikinta tayi out uot ɗin tularenta ta kowanne lungu na jikinta da turaren, ƙamshin shi ya baza room ɗin kai tsaye. Don hatta asha anum dake ƙoƙarin fita seda ta tsaya tana mata mitar kodai kodai. Guntun murmushi kawai meerah tayi tana kama sumar kanta ta soma gyarawa kana ta busar da ita wata farar scap ta sanya tana miƙewa don neman kayan da zata sanya. Tana mirza door handle ɗin ana mirzawa ta woje ma hakan ya sanya anum asha ja da baya tana be me koƙarin shigowan dama. Ido biyu tayi da wannan turɓunau ɗin sunan data be AK ɗinmu kenan. Ba tare daya sake kallar inda take ba ya furta. "MEEFRAH Fa?" "Tana ciki" ta bashi amsa a gajarce tana wucewanta. kansa ya sanya yana shiga bedroom ɗin a kuma daidai loƙacin da take ta ƙoƙarin ganin hannunta yakai kan hook ɗin sabuwan brazia'an anum asha. Tsai yay yana kallonta se wani ɗukawa take tana ɗagowa duk a koƙarinta na son ganin ta ɓalle sedai ta kasa hakan kasancewar kaɗan da bra ɗin ya mata. A natse ya isa gareta ba tare data san yana a wurin ba, amma karon farko wannan shegen mayen ƙamshin san da sam baya taɓa ɓoyune taji ya shiga kanta,unique ƙamshin da har ta mutu tabar duniya ba rata taɓa mancewa dashi kasancewar ta cuɗanyu dashi ba karo ɗaya ba. Sauƙan hannuwansa kan soft gadon bayanta ne ya sanyata buɗe idanunta tana zubama hannun gold eyes nata. Ɓalle mata hook ɗin yay tare da juyota tana fuskan tanshi. Idanunta tayi saurin mai dawa tana kullewa ƙam ƙam jikinta na ɗan soma rawa, shi kuwa saman ƙirjinta ya zubawa ido da suka ɗan ciko kasancewar bra ɗin ta mata kaɗan. Wani abu yaji na yawo a kansa da tunaninsa janyota jikinsa yayi yana mannata da jikinsa unique ƙamshinsa da nata na cakuɗuwa. Luff tayi a jikinsa don ita kanta wani abu me kama da kewa taji yana kamata na rashin jinsa jikinta iyaka jiya kaɗai, Kansa ya ɗora saman haɓarta yana cusa hancinsa cikin wuyanta. Wani numfashi yaja yana kai hannusa ɗaya saman fuskanta gently yake shafan fuskan, ɗayan kuma yana mata covering ta hanyar zagayeta dayay. Lips nashi ya ɗora saman lips ɗinta kafin yayi yunƙurin woni abu yaji ta zame lips nata a nashi tana tura harshenta cikin bakinsa saurin gyaran riƙon dayay mata yayi yana amsar nata harshen da nata yana naɗewa da nashi kana ya shiga bata wani kalan tsotsa na musamman. Hannuwansa na yawo a duka sassan jikinta. Ƙafafuntane suka zoma kasa ɗaukanta na fin ƙarfin tunaninta da taji abun na nemanyi, saurin tarota jikinsa yayi yana zama tare da ɗorata saman ƙafafunsa. Romance na juna suke sosae wanda da duk kan alamu ma suka manta a inda suke a kuma wacce duniyar suke bathtube ɗin da dama tana kan waist nata ne ya shiga mirzawa yanayin ƙasa dashi. Saurin dakatar dashi tayi idanunta da suke cike taf da ruwan hawaye ta ɗago tana zuba masa, wani kalan jann nashi yay luuuuuuuu sakamon neman fita da tafiya da numfashinsa yaji zaiyi duk a loƙaci guda. "pls anam ka fita, kowa ze iya shigowa ya ganmu *AMOUR!*" ta yi maganan idanunta na ƙarasa janyewa tana medasu ta kulle abinta sega ruwan da suka tara na gangaro saman kyakykyawan face nata. dakatawa yayi chakk zuciyansa na ƙoƙarin fasa ƙirjinsa ta fito numfashi me ƙarfi yaja gami da dunɗule yatsun hannunta dake cikin nasa domin duk yanda yakai gajin matsanancin bugawar da zuciyarsa keyi, Sam bashi da ikon buɗe idanunsa dan kallon abunda yake so. Idanunsa da suka ɗan ƙanƙance ya sauƙe akanta as unexpected, numfashin dake cakuɗe da ƙamshinta ya shaƙa tare da karyar da wuyansa gefe, anutse ya tsaida kyawawan idanunsa akan innocent face nata baya ko ƙyaftawa. Musamman ma ruwan hawayen dayaga suna bin idanunta da suke gangarowa. Wani kalan kallo ya shiga binta dashi na musamman tamkar wanda bai taɓa ganinta ba, tun daga kan fuskarta har zuwa kan dogon wuyanta da kuma ƙirjinta wanda ta sanya hannayenta ta kare. Ahankali kuma ya dawo da kallon nasa kan siraran laɓɓanta haɗi da straight noise nata. Haka ya shiga ƙare mata Kallon ƙuri na tsawon wasu mintuna kafun ya lumshe idanunsa asanyaye, saboda wani baƙon abu da yaji yana yawo acikin jikinsa da kuma kansa tattare da abinda yakeji akanta. Wani iri abu ne me kama da tunani ko kuma muce buƙatuwa. hannunsa yasa yaɗan bugi kansa saboda sauyin da yakeji acikin jikinsa, like prabhas ɗin nan idan zazzafan soyayyan anushkashetty ɗinsa ya ratsa shi lol😀 ajikinsa yake jin komai ya sanja masa kamar bashi bane wani ne aka sanja dashi. Bugun zuciyarsa harma da yanayin fitan numfashinsa ji yake yi duk sun sanja an sanja nashin. Komai ganinsa yake daban gyara riƙon dayay mata yayi tare da ƙoƙarin tura hannunsa saman ƙirjinta data kare da duka hannuwanta biyun, ƙamm yaji hannunsa riƙe a cikin nata ta hana masa damar hakan. Lamo yayi haɗi da sake kafeta da idanu bayan ya maida kansa ya jingina da royal chiar ɗin dake gaban bed ɗin. Hannunsa ɗaya ya sanya yana tallafar face nata ruwan hawayen da yake sake gangaro mata yabi yana lashe su. Hakan dayay mata shiya matuƙar sake kashe mata jiki,ahankali cikin rawar da jikinta ya ɗan soma ta buɗe idanunta da nashi yake kan nata yana aikin lasar hawayenta da suke sake saƙkowa. kasa ɗauke natan tayi domin ji tayi kamar bata taɓa ganinsa ba, ko kuwa ta share lokuta me tsawo bata sashi acikin idanunta ba tamkar ba iyaka jiyan bane basa tare. Kewarsa da tayi da kuma irin abubuwan da taji akansa a daren jiya kawai da basa tare suka shiga dawo mata, wanda hakan yasa ta ɗago hannunta dake rawa ta sanya tana ɗora nata tafin cikin nashi, ɗayan kuma tana zagayo waist nashi. Ɗumin hannunta da nasane suka haɗe wuri guda wanda hakan ya tilasta mata sake jin karyewan zuciya, wanda kai tsaye hakan ya sake ɓallar mata da ruwan hawayen dake cike taf a idanunta. Ita kanta ba zatace ga sanda hakan ya faru ba tasan dai kawai tasan ta sake matsowa kusa dashi, haɗi da damƙe lallausan tafin hannunta acikin nasa ta haɗesu ƙam. Cikin wani kalan muryan dake bayyana haƙiƙanin abinda ke zuciyarta ta furta. "Nayi kewanka Amour! Nayi kewanka sosai A iyaka daren jiya da bakanan komai ba daɗi na tashi bana farin ciki na kasa iya bacci, haka ma na kasa iya cin abinci komai na jiki na yaƙi bani haɗin kai wajen motsawa ata dalilin ka Amour!!" Ta ƙare maganan tana me sulalewa a jijinsa data gama illata komai nashi. Ba zai iya jurarn wannan yanayin ba tabbas don haka yay saurin haɗe bakinsu gudun kada abinda be taɓa faruwa dashi ba ya faru yau. Shi kansa be taɓa sanin shi mai raunine har haka ba se a kanta?, be taɓa sanin cewa shi *ABDOUL MALEEK HASSAN AL-HASSAN EMAAR's* ze taɓa iya sanin cewan zuciyansa zata kamu dason wata mace ba se a kanta. A cikin shekarun da basu gaza ɗaya zuwa biyu ba se gashi ta sanja tunaninsa kawai cikin farkon ganinsa da ita.Wannan haɗuwan ta farko itane ta sanja rayuwarsa izuwa yanda yake ayanzu, wanda zanen ƙaddarar da baya taɓa gogewa ya buɗe tsaƙiyar ƙirjinsa ya rubuta masa sunan Meerah acikin ƙahon zuciyarsa. ƙaddarar dake wahalar da rai da kuma numfashinsa. Wani kalan kyakykyawan runguma ya mata yana rasa ma abinda ya dace ya mata se kawai ya sake rungumeta jikinsa. Yana bin ko ina nata da wani kalan kyakykwan romance na musamman. Sun ɗauki loƙaci me tsaho suna romance na junansu ƙaran door belt da aka danne shine ya farkar dasu daga duniyar gajimarwen da suke shirin lulawa. A matuƙar kasalence da kuma mutuwan jikin ya janyeta a jikinsa yana shigewa bathroom seda ya ɗauka good ten mints kana ya fito fuskanshi da damshin ruwa ta inda allah ya temake shi ma ɗayana shine kananun kayane jikin ba masu nuna secuzing ba da duk kalan gyarawan da zeyi bazai koma normal nashi ba. Danim jacket nashi ya ɗora a saman kayan yana maida pcarp nashi ba tare da yayi gangancin kallon inda take tuƙunƙuneba yasa kai yana ficewa fuskarnan mur ya an manta kunun da ba'ai mai haɗi ba. Da kallo anum asha ta bishi tana taɓe baki ganin uban zaman datai wurin meran ƙarfe wato ash amma wai har haka yana maƙale a ɗakin. Ak kuwa daga nan kai tsaye aiport ya wuce se Kuwait ɗinmu ta gaɗo. Ɓangaren anum kuwa kallo ɗaya tama meerah ta ɗauke kanta ganin yanayinta woni abu makancin shuɗaɗɗen wani lamari na ƙoƙarin kusantowa gareta. Kanta ta taka tare sa toshe kunnuwanta tana furta "NOH!!!" da ƙarfin daya sanya meerah tashi a har gitse. Kanta tayi tare da rungumarta tana furta. "Pls kiyi ƙoƙarin goge komai asha!" kasancewar lajja ta basu labarin ƙaddararn daya kusan ristawa da Asha anum ɗin. A dalilin kusan mata faiɗe da akayi Allah ya temaketa hakan be barufa sedai kuma hakan yayi sanadiyyar taɓa brain nata, lufff tayi a jikin meerah ɗin tana jin rawan da jikinta keyi na ragewa..... A washe garin ranan Jedderh tabar madina tana komawa makka wurin mahaifinta da dama dauriyace kawai yake abinka da jikin tsufa wanda ya cakuɗu da ilimin addina ne ya sanya yake daram ba gare da ya sami taɓuwan kai ba. In banda haka ko ita kanta jedderhn tare da lajja su kansu sun manyanta. A loƙacin data isa har yana hospital don haka kai tsaye cenn ta wuce tare da zeeneeh data mata rakiya. Tana zaune gefen gadon da yake kwance hancinsa sanye da abin ƙara numfashi. A loƙacin daya buɗe idonsa ya sauƙa akan Jedderh tare da Mah seya haɗe duka hannuwansu biyu yana duban Jedderh, cikin ƙarfin hali da ƙoƙari ya shiga furta. "Ita ƘADDARA da kike gani ZEYATOUL HUMEIRERH na ɗaya daga cikin hukuncin da allah subhanahu wata'ala kan zartar akan ko wanne bawa nashi kai tsaye ba tare da ko wacce irin tangarɗa ba. haka nan tamkar zagayen zobe take wanda ɗan adam ke rayuwa a tsakiyarsa, idan aka ce ƙaddara ana nufin duk wani abu da zai samu bawa tun daga ranar haihuwarsa har zuwa ranar da zai koma ga mahallicinsa sunansa ƙaddara. Kana tana rubututa maka zanenta ne tun kamin mutum ya zo duniyar duk iya gudunka duk iya saurinka kuwa baka isa gujema tarin ƙaddarorinka ba. Domin ko wanne rai me numfashi da ka ga yana rayuwa a doron duniya to yana yin ta ne a doron ƘA DDARARSA.Haka kuma ƙaddara na ɗaya daga cikin manya manyan siffoffin Allah subhanahu wata'ala,domin ita kanta ƙaddarar ba kowa rai me numfashi Allah ke jarraba ba se ran da ya cika mumini. Don haka ina son Ki ɗauki hakan a matsayin jarabawarki ZEYATOUL HUMEIRERH!!! Kana ko wacce ƙaddarata tana da madubi kedai naki madubin sune *ABDOUL-MALEEK* da *MERYEMERH* sune madubin taki ƙaddararn, Aurensu kuma shine mabuɗin hasken EMAAR's....... Se kuma tari ya sarkeshi amma be saki hannun suba cikin ƙarfin hali yaci gaba da faɗin. "Alhamdulillah ko yanzu na mutu nayi farin ciki domin kuwa zan kaiwa khairy kyakykyawan labarin ganinki da nayi! Ki rungumi duk wasu sauran ƙalubalen da zasu biyo baya don ƙurar bata ƙare ba! Komai bezo muku ƙarshe ba amma idan kika imani da sarkin sammai bakwai ƙassai bakwai se abin yazo muku da sauƙi. Dominwasu sun naɗe a bayan rigar wasu amma a sannu duk wani mugu ze bayyana kansa ta hanyar samun wani hasken dake daf da zuwa duniya don yanzu haka anyi ƙyanƙyasarshi haifarsa kawai ake jira aje aci gaba da gayawa ALLAH shike maganin komai........ A cikin ƙahon zuciyarta take ayyana lallai duk waɗan nan tarin abubusan duk sun faru ne sanadin cewa ƙaddararsu hakan tazo musu. ƙaddarar da babu makawa saita faru.Numfashi taja tare da sakin ƙaƙƙarfar ajiyar zuciya, ahankali kuma cikin yanayin dake nuna cewa tayi believing da ƙaddarar da Allah ya tsara musu tace kuma lallai da akwai hikimar Allah nayin hakan. "Habibullah na daɗe da amsan wannan ƙaddarar tun a loƙacin dana buɗi ido na ganni jingine jikin matashin damisar jinina wanda shine yay sanadiyyar bayyanar duka haskenmu baki ɗaya, na dena tsoro da fargabar komai addua kuma kullum cikin miƙawa Allah kuka muke Allah ya huce mana gaba badon halinmu ba!" Ta faɗi wasu hawaye na kwaranyo mata daga nan kuma manyan likitoci suka ce su fita mara lafiya yana buƙatar hutu. Hannunsa ciki na jedderh daƙyar aka zare hannun duk se taji bama tason fitan ta barshi, se taji tana son dawwama a hakan riƙe da hannuwansa . A reception na hospital ɗin suka zaune jikkunan su duk a sanyaye sunajin duk ransu babu daɗi. Kamar kuma daga sama sega likitoci manya suna rige rigen shiga ɗakin da suka fito wanda mahaifinsu ke ciki. A matuƙar ruɗe suka mike hannun Razeenerh jeddarh ta ɗamƙa a nata. Se kuma suka soma ganin likitocin na fara fitowa ɗaya bayan ɗaya wasu har kamar na goge kwalla. Hannunta dake cikin Razenerh jedderh ta sake damka ganin wani likita na nufo inda suke, kanta ta soma jujjuyawa tana ja da baya baya tare da soma fadin. "Karka min magana! Karka ce min komai domin bazan iya ɗauka baaaaaa... Ta faɗi tana yin baya luuuuuuuu *BY AMMEYLAYLERH* MU KWANA LAHIYA SAFIYA TA GARI MUTANEN AMANA..... *🦅 MIKIYA 🦅* _A wonderful world & Special anti terroRism squad_ ____________________ *MARYAM NASEER MIRRAH* ~AMMEY LAYLERH ✍️~ ✯ *~🌠 JAJIRTATTU WRITER'S ASS.... 💫~* BOOK Two…………………………񆬍✍ # Hot Romance scene # Real life # Hot love scene # Ak meerah # A.k.a AMMEYLAYLERH👍👉 *Bɪꜱᴍɪʟʟᴀʜɪʀ Rᴀʜᴍᴀɴɪʀ Rᴀʜɪᴍ* ♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡ ★ 37&38 Saurin tarota Razeenerh tayi ta faɗa jikinta itama tana jujjuyama dactor'n dake sake kusan tosu kai. "Ahhh A ahh! Ba buƙatar kayi magana don wllh nima bazan iya ɗauka ba!!!" Razenerh ya faɗi tana sulalewa ƙasa da jeddern Ashaan jikinta. Wani kalan murmushi me ciyo Doctor yayi hawaye na zubo masa cike da tsananin tausayinsu ya furta "I'm sorry to say *SHEIKH ALIYULLAH DAWOOD* is gone sai Mun yi haƙurin rashinsa mutuwa rigan kowa ce" ya faɗi yana juyawa yanufi wani office don turo norses suzo su kula dasu mah. Wacce itama yana faɗin hakan kanta ya saki ya langwaɓe alamar numfashinta ya tafi hutun wucin gadi itama. Cikin gaggawa sega manyan norses mata suna temakawa su jedderh. Wani special ɗaki aka sanya su kasancewar sa mutum babba a ƙasar tuni sega rasuwarsa har an haska cikin abinda bai wuce ƙiftar idanu ba sega wannan hospital ya cika maƙil da ƴaƴa da jikoki har dama tattaɓa kunne. A loƙacin da aka haska mutuwar Sheikh Aliyullah a daidai loƙacin lajja da Anne dama raiha suna a yawon zaga dangi ne. Babu wanda ya lura se ganin lajja sukay bata tare da numfashinta. JALAAL ASH ne yay gaggawan ƙiran woyan lajja yace su dawo gida gudun kada takalla mutuwan mahaifinta a tv, sedai ya makaro a loƙacinma bata numfashi hannuwan Anne na rawa itane ta amsa woyan. Jin anne ce ya sanya gabansa faɗuwa kaɗan "Laj..... Tun kamin ya ƙarasa anbatar sunan ta katse shi ta hanyar furta. "Bata numfashi!" Kansa ya ɗan rike yana furta ohh god, se kuma ya tambaya inda suke kanta taɗan jujjuya alaman bata sani ba tunda ba ko ina ta sani ba se kuma ta manna woyan a kunne ɗaya daga mutanen da suka zagaye lajjan. "JALAAL Lajja tana tare damu" wacce ta bama woyan ta faɗi hakan kawai tana bata wayar. Amsa tayi tana meda woyan kunnenta tare da furt, "Ka gane inane muku J ?" ta jefa masa tambayar. "Ehhh ganan zuwa kuna gidan Jadda Malika ne!" yana faɗar hakan ya datse ƙiran tafiya bame yawa ba yayi a motanshi yazo gidan kai tsaye tare da zayeed ash ya taho. Bayan sun ɗauketa gida suka koma da ita seda aka bata taimakon gaggawa kafin subi jirgi xuwa makka ita dasu anne da Oum Asha anum, da dai duk wanɗa da suka kamata harda abiderh matar zayeed duk da tana fama da jikinta kasancewar bata da cikakkiyar lafiya. Da har anne tace ba se anje da meerah ba amma JALAAL ash yace suje da ita tunda harda anum zataje itama. Baki ɗaya ko wannensu baya a cikin mood me daɗi da sun tuno moment nasu da tsohon kuwa se kowa ya ɗauke kwalla barin ma anne data rungume shi ɗin nan yace _Ashhh zata karasa ɓalle muku tsoho fa umami_ wannan maganar da anne ta tuno se kawai hawaye su sake ɓalle mata da kuma yanayin zafin jikinsa da taji a loƙacin. Cikin wasu ƙananun mints suka isa makka. A loƙacin manyan malamai da manyan yaransa maza guda biyu harsun suturtashi, kasancewar zuwar wuri sukay ne ya sanya suka sama ganin gawar inda anne da lajja suka sha kuka sosae akan gawar kana suka masa adda'oi sosae daga nan aka miƙa shi ga gidansa na gaskiya. _Sedai muce sheikh Aliyullah ubangiji ya jiƙanshi da ramaha yasa yayi kyakykyawan ƙarshe, idan tamu muma tazo yasa mu cika da imani ameennnnn_ A take Ak ya juyo don ko zaman 30 mints beyi ba kuwait, Oum kawai ya ɗauka kasancewar dama Paah ɗinsa yana cannn tare da jeddern shi. Shima ya sama suturar sheikh ɗin da sosae yaji mutuwarsa don mutum ne me iya mu'a mulantar mutane, gashi da bewa da kuma tattako irin na dattijan kwarai. Shi ɗin renonsa ne shiya reni shi shine da kansa ya fara koyar dashi karatun addini shine wanda ya fara farkar dashi tare da haskaka masa hanya, don kar yabi ta cikin duhun duhuwar da mahaifinsa yafi. Shine mutumin daya bashi wasu sirrika manya kana ya turashi xuwa ƙasar nigeria ta hannun manyan malaman ƙasar, wanda kai tsaye yaje a matsayin soldier bayan an maida mishi komi nashi xuwa na ƙasar sunan kuwait ne kawai yace bazai iya sanjawa ba. Kasancewar shi me kishin ƙasar sane kafin wasu matsaloli suka kunne kai harya fice a cikin aikin soldier's ɗin wanda kai tsaye hakan duk a cikin tsarin sune. Kai idan yace tsohon shine komai da komai nashi samm yasan beyi ƙarya ba. A daren ranar ya shirya ma Malam Abdullahi zuwa kasar makka tare da Hajjia umma wacce ta reni Anne tamkar ƴar data haifa. Kowa besan da zuwan nasu ba har ita kanta annen. A loƙacin da bappa yaje ma da hajia umma da zancen tafiyar sosae tayi mamaki kenan dai Anne ta ko ina gaba da baya ita ɗin ƴar gata ce ta gaban kwatance. Domin dai kowa yana jin sunan wannan shahararren malamin kuma limamin makka wato Sheikh Aliyullah Dawood ashe shima kakantane. Wannan shi ake ƙira da ikon Allah. Abokan zamanta kuwa zarewa ne kawai basu ba a loƙacin da bappan yaje musu da batun anyo masa visa shida hajia umma zasu tafi ta'aziyar kakanta daya rasu sheik Aliyulla. Jin an anbaci sheik ɗin kawai nan ba ida rikicewa jikinsu yayi don already sun kalla mutuwan mutumin a labaran BBC arewa. Irin cika da tumbatsar daya samu ya jama'a kaɗai abin girgiza zuciyar maƙiyine, Sarkin makka da kansa shine riƙe da makaran da aka kaishi ta gaba ta baya kuma sarkin madina mahaifi ga Anne wanda mutane suka ta zumin iyaka face na ash tare da haɗawa da pisc na meerah a irin wanda Salman ya saki a media ana ta tofa albarkacin baki. Gaba ɗaya a cikin satin labaran da suka zama tarend kenan suka zama latest aka haɗa fuskoki uku MEERAH,SARKI ASH,SHEIKH ALIYULLAH DAWOOD, da ɗan ƙaramin rubutu kamar haka. *_SHIN ME MUTANE ZASU IYA CEWA DANGANE DA WANNAN LABARIN?,WANNAN SHAHARRIYAR ƳAR JARIDAR NAN MARYAM ABDULLAHI GWANI, WACCE AKAFI SANI DA *MEERAH* JIKACE GA ME GIRMA SARKIN MADINA ASH, KANA JIKA GA WANNAN SHAHARARREN MALAMI KUMA LIMAMIN ƘASAR MAKKA. SHIN ME KUKA TUNANI DANGANE DA HAKAN?_* Tuni amsoshin mutane a comment section sama da million dubu goma yay ca akan kafar sada zumunta ta Zamani TV da suka haska labaran. Wanda kai tsaye Disha ce ta bada baya nan. Bayan ta gama gano komai itama se kuma a jiyane ta sake samun ƙarfaffan hujja daga hajjia umma. Haka mutane suka ringa maida martanin amsoshinsu, wasu suce shi yasa taƙi bayyana kanta kenan saboda tasan ita ɗin jinin manyace. Wasu kuwa Martanin zagi ne wasu kuma suna bayyana irin tRin soyayyar da suke ma Meerah. Haka dai duk inda ka ratsa zancen akeyi ko ina da ina. ★ A washe garin ranar bappa da hajia mama suka nufi Makka, tarɓa ta musamman suka samu daga families na Anne. Kwarai sunji daɗin yadda aka karramasu wanda ko ɗaya basu zatan zasu samj irin wannan kyakykyawad tarɓa daga garesu. Bayan sun gama gaisawa aka shiga nunama dangin Anne da matsayin data bata.nan kuwa aka shiga mata godiya sosae bappan ma yashigo sun gaisa da mutanen cikin gidan. Queen lajja da mah se nan nan suke da bappa da Hajia umma, Bayan sarakar uku Oum da Ak suka kuwait.... Kuma duk kwanaki ukun da sukai AK be sama ganin Meerah'n shiba, Haka ya koma da kewar rashin ganinta da baiyi ba. Amma ya danne hakan ko alamun nemanta ba beyi ba ma. Haka sukaci gaba da amsan zaman makoki harna tsayin kwana bakwai, A ranar kowa ya kama gaban adda'ar da yasha. Anne lajja ce ta koma da ita, ita kuma meerah mah ta wuce da ita kuwait, a ƴan tsakan kanin kwanaki bakwai ɗin nan kuwa sosae ƴan uwan Anne suka sake gyare mata meerah ɗinta ciki da waje ga tsumin Shu'umar humra da sauran kayan dumama jiki. Sosae a cikin kwanaki bakwai ɗin ta sake mirjewa fatar nan har wani kalan glowing na kyau da ɗaukan idanu take. Hatta gashin kanta da tufa tufanta seda aka tsumasu da tutaren wuta kala daban daban. Dake duk se yamma kowa se kama gabansa. Har dama hajiya umma suka koma bappa nedai yace su batshi anan don ze tsaya ibada a makan. Hajiya umma kuwa binsu tayi Mah se nan nan takeyi da ita har suka sauƙar kuwait. Se dare suka sauƙa a ɓanharen Razzenrh suka sauƙa seda suka gabatar da sallan isha'i kana suka nufi dining area Wanda Oum ta haɗa musu kyakykyawan lonch me rai da lafiya, diner sunkayi. Bayan Oum ta shigo sun sake gaisawa, take sanar musu tana son a miƙa Meerah ɗakinta haka nan wato Apertmen na Ak kenan. Mah tace ba komi suma dama sun riga sun tsara da Queen lajja tare da Jeddern Ashaan. Sosai Oum taji daɗin hakan da suka mata a washe garin ranar Mah ta sanya aka sanja komai na ɓangafen Ak ta zubama meerah komai disigner's masu rai da lumfashi. Wanda dama already ta riga ta gama magananta da masu fenicture's. Wata ƴar kwarya kwaryar malima suka haɗa da misalin ƙarfe biyar ɗin ranan, yasu yasu sukai waliman inda meerah tasha ado da gwala gwalai, gefe guda kuma ga wasu shegun Kit masu shegen kyau da tsada har set shida ko wacce kalo ɗaya me bakwai ce haka oum ta haɗa kayan. wanda kuɗaɗen da aka narka kawai wajen siyanta se abin ya baku mamaki na gaske bare azo kan uban kayan da aka zuba wanda ya lashe kuɗi wajen kimanin Billions of nera. Dom ina ambatar kuɗin nan kwakwalwan wasu ka iya juyewa kawai kuui emeg akwatu set ɗeɗe har bakwai, kana ko wacce set ɗaya tana dauke da guda bakwai. Sosae suka gudanaf da taron walimarsu cikin aminci da jin daɗi daga nan meerah aka dangan tata da ɓangaren Ak, kuka sosai tayi kan itafa ba zata zauna anan ba seda ta koma wurin OUM,ko ita mah ɗin. Ko Jesrah seda mah ta mata jan ido kana ta saduda tahaƙura...... ★ _Nigeeia *Kano* Tun daga bakin shi ga Countrol Room ɗin zaka fara jin kayaniya ta mutane daban², sedai wasu muryoyin sunfi wasu muryoyin yin sama. "Lallai tabbas ya zama dole mu kawa ƙarshensa a cikin wannan tafiyar domin duk aikin da fara ƙarshe shine yake fara ɓata mana, da wannan baƙar zuciyarsa! To Allah na tuba ma yanxun waye yake tsayawa yay ma mutane aikin tsakani da Allah?, Su mutanen da kake fara karewa daga ƙarshe suna masu kwayema baya ba zasu duba irin talin halacci da sadaukarwan daka musu ba. to duk miye amfanin wannan kunga kuwa kwara ka tsaya ka mori ƙuriyarka da loƙacinka amma ya zama dole mu kawo ƙarshen Kamaal a wannan karon." Dcp ya faɗi ransa na sake ƙuna domin wani aiki da suke yi akan case ɗin wata yarinya da akayi rep nata. So kuma ɗan gidan mataimakin gwamna shi ne yayma yarinyan fayɗe daga bisani kuma ya kashe ta, shine fa iyayenta suka shigar da ƙara, su kuma gwamna da mataimakin gwamna suka baza kuɗi kan karsu yadda sunan ɗansu ya ɓaci. Shine shi kuma kamaal ɗin ya jiƙa musu aiki ta hanyar fara binciken sirrin daya fara, kasancewar sune gwamnatin ya sanya tuni maganar ta shiga kunnuwan gwamna da mataimakin gwamnan, shine suka bada umarnin asheƙe shi kawai kai tsaye. ★ *Kamaal Pov* Kasancewar duk ranar yau be fita bane kasancewar hutu da suka bashi na 2week. Haka suka wuni ƙauna shida mariyanshi da kuma onborn ɗinsu da bai riga da yazo ma duniyar ba. Kamar yanzu ma tana kwance kan ƙafafunsa basu jima da dawowa daga gidan suba da kamaal ɗin shiya buƙaci da suje da kansa. hannunsa dake kan cikinta da yasoma girma itama ta ɗora nata saman nasan tana sakin ijiyar zuciya. Fuskanta ya ɗan shafa yana ajje Littafin *MIN HAJJIL MUSLIM* dake hannunsa yana gyara mata kwanciyarta a jikinsa. "Kwana biyun nan fa duk mrs aiy ta damu Aiy nata da son jikin nan nata sosae" "Kawai nima naji inason hakan hakan! Jikina ne nake jin duka babu daɗi a cikin kwana kin nan wllh, ga yawan faɗuwan gaba duk sena ji jikina yayi sanyi sosae wllh Soyayyata!!!" Ta faɗi cikin raunin murya har wasu guntun hawaye na saƙƙo mata. Wani ɗan guntun murmushi yayi yana faɗin, "Ba wani nan kedai kawai son jikinki ya motsa dai ne madame" sake kanƙamesa tayi tana sakin kuka kawai tare da faɗin "Allah da gaske nake ba da wasa nake ba Yaya Kamaal! Samm sammm bana jin daɗin jikina da yanayin, se nake jin tamkar woni abu daga sashe na jikinane ke shirin barina ko rabuwa dani na har abada yaya" Ta yi maganar in serious hawaye na zubar mata.jin sunan yaya data ambata ne ya sanya shi ɗago kanta cikin wani tattausan sauti ya furta "Miye kuma na kukan? Kuka baya miki wuya ƙo mr aiy?na rasa dalilin dake sanya min mata kuka" kanta ta sake jijjagawa dan ita kanta bata san dalilinta nayin kukan ba kana ba zatace ga abinda yake sanyata kukan ba. Hawayen fuskanta ya shiga share mata yana faɗin. "To bana son wannan kukan don Allah kimin alƙawarin ba zaki min wannan kukan ba adda'a itane maganin koma menene ba kuka ba. A duk sanda kikaji tsoro ko faɗuwar gaba ba kukan ya kamata kiy ba yi koƙarin danne su da ambatar Inna lillahi wa'inna ilaihir raji'un wannan kalmar yana samar da nutsuwa mrs aiy!" ya yi maganar yana jin yadda gabansa ya buga a loƙaci ɗaya amma seya shanye hakan yana kawar da tunanin dake son bijiro may. Don ma gudun kada ta fahimta komai tattare dashi ne ya sanya shi miƙewa bayan ya gyara mata konciyarta yana me ce mata Bara yaje mosque ya dawo. Har yana tsokanarta wannan Ko kafin ya dawo cikin ƙarfin hali ta ɗan shirya masa wani guntun kirki sama sama shima ta soya may wainan kwai da tea. Daga nan wanka tayi itama ta gabatar da sallar isha'i ta sanja kayanta xuwa wasu riga da wando dogaye marasa nauyi sosae sky blue. Palon ta koma tana zaman jiran ya shigo babi jimawa kuwa se gashi ya dawo, daga zaunen da take ya cirata ita da jikin jikinta yana zaunawa mazaunin da take yana ɗaurata kan ƙafafunsa ita kuma. Da ƙafanshi yayi amfani wajen janyo dining ɗin data gama shirya may dinner. Haɓar ta ya ɗago tare da kallon cikin tsaƙiyar idanunta dake azabtar dashi. "Me abin mamaki ko?" ya faɗi yana lakuce hancinta. Duk yadda yaso da taci ta gaza cin abincin shi kuwa yaci abinsa daga nan ya ɗauketa kai tsaye yana yin bedroom da ita, yana faɗin. "Zo muje yau daren na musamman muje mr aiy taji da mrs aiy ɗinta" ƴar dariya kaɗan tayi waccs kawai ta yake ce don ita kaɗai tasan kalan gashin da take amsa daga cikin zuciyarta ƴan kawanakin nan. Sosai suka raya daren da tsabtatacciyar soyayyarsu me rai da lafiya. Washe gari ma haka ta tashi da yanayin mutuwan jikin nan har yake tambayanta kodai cikinne ke sanyata jin hakan se kawai ta faɗa jikinsa tana sakin kukan da duk tayi yake jin tamkar yankar zuciyarsa ake. Ko a wurin aikin daya fita wanda yaune ya dawo bini bini ta ƙirashi taji wai ko lafiyansa kalau. Se kuma ta kara wayan da cikinta tace motsi yake shima yana son yaji sautin bugun nimfashin abiey'n shi. Ya kan yi dariya mara sautu ya kashe wayan kawai duk yay wanda ya kallesa da wannan murmushin yake kallonsa, Duk wasu shedu kuwa ya gama tattare abinsa wuri guda a ranar ya tafi dasu gidansa bayan ya biya ta wurin office ɗin Dsp. Inda dsp ɗin ya sake gargaɗansa akan ya janye batun case ɗin nan na yarinyan ma da bata raye bare ayi shari'an har gaskiya tai halinta me ita ya ɗauka. "Kai a ganinka kenan, ni barazana wa mutuwata ba baƙon abu bane a wurina!, don ba jiya ba ba yauba na saba fuskantan barazana daga wurin mutane maban banta. Don haka tunda har na riga na fara aikin nan nake ga babu barazanar data isa sawa na janye batuna akan masu gaskiya se ko in mutuwa nayi bi ma'ana kuka sanya aka raba numfashina da gangar jikina!" se kuma ya ɗan dakata tare da fesar numfashi. "Se dai kashe ni a tafiyar ba shike nufin kawo ƙarshen azzaluman mutane da gurɓatattun jami'ai irinku ba sir' akwaisu akwaisu akwai dubinsu masu zuciyar lu'u lu'u da ɗanyen gwal, duk da shi baya da runduna ko ayari domin kawar da magauta azzalumai amma a ko ina bila adadin wannan kamaal ɗin dake tsaye gabanka har abda shi kaifi ɗayane kamar yadda zafin kansa be taɓa barin ya aikata ba daidai ba. Kashe kamaal kuma na nufin kun gayyatoma kanku da kanku goran gayyatar tonuwar asirinku da mutuwar kune wa AK!!!" "Tabbas se a yanxun na fuskanta komai malam kamaal kace ashe linkin ba linkin ɗin maƙudan kudaɗen da muke amsa daga matai makin gwamna fiye da hakan shi kake amsa daga wurin babban crime irin Wannan tantirin AK ɗin" dsp ya faɗi yana wani shafar munafukin ƙasimbarsa da katon cikinsa dake rawa shima, sw kuma ya kece da wata kalan dariya yana furta "Ashe dai masu fatar akuyan yawa garemu kawai ka faɗo cikinmu kaima sunanka yay shura da ƙauri a baki ɗaya jahar kano harma da kewayenta kamaal" Idanunsa ya rumtse da ƙarfin balai tareda da bugar teburin gaban dsp cikin ƙarajin murya ya furta. "Har abada In banyi adalci wa ƙasata da kuma aikina a matsayina na jami'a ba, zuciyata bazata taɓa samun nutsuwa ba a yayin dana buɗi ido na kalla ana aikata wata ɓarna, kasa cin abinci nake haka kuma kasa barci nake ni banyi kama da jami'a ɗan rufa ido ba ni ɗin *KAREN TSAYE NE* wanda baya lankwasuwa ta daɗi se anci kashi domin duk wanda yay ko yunƙurin lankwasa shi ne to ku sani gefe dashi akwai gidan rinar dake dabaibaye dashi domin bashi kariya daga gurɓatattun ƙasa irinku!!!" "Waye shi?" dsp ya tambaya. "*THE MAN WHO CANNOT DIE🙄* *AK, EAGLE Mutumin da baya mutuwa, haka baya da tsoro domin shi kansa tsoro AK firgitashi yake" Yana faɗin hakan ya fice a mugun fusace yana banko masa ƙofar office ɗin, wata mahaukaciyar dariya Dsp ya saki bayan yayi ya gama kana ya ɗauki wayarsa ya ɗanyi waya me tsayi kana ya ci gaba da dariyarsa yana barin office ɗin shima. _A wannan daren komai ya faru rubutacciyar ƙaddarar da aka sanya alƙalamin da baya ƙarya aka zana wa'aɗin da aka ɗibarma wannan ruhin ya cika sedai akwai sanadi!!! Ehhhhh tabbas akwai sanadin hakan mujeeeee_ *A DAREN RANAR* Suna kwance da misalin ƙarfe biyun dare taji ya farka a firkice wanda itama hakan ya sanyata farkawan a tsorace don dama duk a tsoracen take. Cikin muryan bacci da kuma tsoro ta ce "mra aiy lafiyanka kuwa?" ta tambaya. "Mra aiy na jiwo ƙaran buɗe get ne" "Get kuma da daren nan kodai kunnen kane, duk ina baba me gadin yake" tayi maganar a sukurkuce don duk ma ta rasa gane kanta. Jikinta kawai rawa yake mata tace "Dan Allah karka fita kasan da me suka zone? kawai ka ƙira jami'anku suzo amma kai karka fita yaya kamaal kawai mu buɗe ƙofar baya mu gudu" "Mrs aiy ina son ki sanya wannan yaƙinin a ranki cewar har gaban abada matsoraci baya taɓa zama gwani, don haka zan fita duk abinda zakiji karki yarda ki fito ko dan wannan ya rayu" Ya faɗi yana ɗora hannunsa akan cikinta daya ɗora hannunsa akan cikin daidai da motsin da cikin yayi. riƙeshi tai ta maƙalƙaleshi tana kuka sosae "Don Allah karka fita yaya tsoro nake ji " "An haifeni ne badon naji tsoron mutuwa ba MARRIYERHTOU!" An haifenine domin kawi ƙarshen baragurbin cikin al'umma ki sani kowanne zaki mafaraucine a dawa yayinda aka shigo gonarsa, inason ko wanne irin tsoron dake ranki ki kawar dashi domin ni *KAMAAL RANO* ba matsoraci bane samm banma haɗa hanya da tsoro ba bare nasan ya kalansa ko kamanninsa suke, har abada inason ki kasance jarumar mace ko bayan babu raina Mrs aiy!!!" Yana faɗim hakan ya rungumota jikinsa da ƙarfi. ijiyar zuciya dukkaninsu suka sauƙe zuciyoyinsu na bugawa,A hankali kuma ya sake ta yana sakin wani murmushin da tunda take dashi bata taɓa ganin yayi irinsa wanda yay mai kyau kamar na yau ɗin ba. Sake faɗawa jikinsa tayi hannuwa na rawa ta sake rungume shi ƙam. Bakinsu ta haɗe guri guda inda take jin numfashinta nayin sama sama, da sauri ya janyeta a jikinsa ya na fita. Numfashi me ƙarfi ta saki loƙacin daya fice a bedroom ɗin. A hankali ya fito ya soma tafiya cikin sanɗa, ga mamakinsa duk seya tarar an kashe duka bubls ɗin gidan har zuwa lungu nan dake bakin get, can ya hangin me gadinsa kwance cikin jini ga kuma karensa dake a daddaure bakinsa rufe da seltif.Motsi yaji ata gefenshi da babu hasken bubls a wajen,ahankali ya maida dubansa yana ƙurawa gurin ido sosae. Inuwar mutum ya gani tsaye a wurin da sauri ya waiga ɗayan gefensa seya kuma hango ɗaya inuwar mutum ɗin.da baya da baya yay hanzarin komawa ciki da sauri ya shiga bedroom ɗinsa, hannuwansa ya sanya yana janwo wata drower ya ɗauko bindiga a ciki ya maida drower'n ya ɗago yana gyaran riƙon bindugunsa. Jikintane ya shiga wani kalan rawa loƙacin da kunnuwansu suka fara jiyo musu ƙararn harbin bindigu. "Koda wasa kida ki sake ki fito koda wasa bazan taɓa barinsu su shigo ciki ba, kinga wannan ƙofar bulletfroof ce harsashi baya fasa ta ki rufe ko ina koda ace sunyi yunƙurin harbi bazai fasu ba ko waye yace ki buɗemar karki yarda ki buɗe idan harba ni bane!" daga haka ya janyeta a jikinsa yana barin bedroom ɗin. Ita kuwa ɗurkushewa tayi a wurin tana sakin kuka sosae. Riƙon bindigarsa ya gyara nan fa ya shiga sakin harbi takan me uwa dawabi haka ya shiga harbin nan, nan suka shiga musayar wuta shida ɓoyayyun mutanen da duka jikinsu yake rufe. Ganin yadda Kamaal ke zubar musu da yarane ya fusatar da ɓarayin nan, nan fa cikin tafasar zuciya suka shiga kaima daga inda yake laɓe harbi, shima a fusacen ya fito daidai da wani daga cikin mutanen ya sami nasarar harbinsa a gefin ƙirjinsa. Cikin haushi da ƙunar zuciya yay gaba da gaba dasu yana fuskantarsu. Chakkk ya tsaya ganin fuskar miles babban yaron AK wanda daga arms se shi a matsayi. Kafin ya dawo daga cikin duniyar mamakin ya sake jin sauƙar wani harbin a cikinsa. Se kuma aka shiga harbin nasa tau tatau tau tau. Har wajen sau biyar zuwa shida. Ƙarar azaba da raɗin ratsa harsashin jikinsa kamaal ya saki wanda karab a cikin kunnuwan Marria, ɗan cikin tane yay wani kalan motsawa yana mata tambulan a ciki tamkar wacce aka zabura kuma ta mike tana ɗaukar wani shiraminsa ta lulluɓe jikinta. Ka tsaye inda taga ya ɗauka bindigar nan ta nufa guda biyu ta ɗauka dama da hagu tana bude kofan, babu tsoro ko jimamin mutuwa ta ratsa ta cikin palukan gidan tana yin woje, duk da wanda ta haɗu harbin kansa kawai take idanu rufe. Don ita kanta ba zatace ga sadda ta iya harbin ko take harbin ba, tasan dai kawai zuciyanta tafar fasa yake yana mata kuna sosae. Haka cikin wani kalan salo tamkar wata soldier take harbin duk wanda taci karo dashi, kamar daga sama kamaal dake kwance cikin jini ya rumtse idanunsa cikin azaba yana jijjiga kansa "A ahhhh! a a No AIY'N! No mrs aiy kar kiyiiiiii! kada kiyi ki koma" ya faɗi da ƙarfi sosae ina ko jinsa bata yi harbi kawai take kuma idan tay harbin bata taɓa gota seti. Guntun mutane ukun da suka saurane suka diba a guje suna barin gidan a350 na karshen ta kaima harbi a kasa nan take kuwa ya zube yana kururuwa, bindigun hannunta ta zubar wani kalan jiri na dibanta ta isa gabansa ta zube. Wani irin kuka ta saki ganinsa cikin jini kwance jikinsa ta faɗa tana sake fashewa da wani sabon kuka. "Sei da nace kar kayi, kada ka fita Amma kaki saurarana mr aiy'n kalla ka gani sun cutatarmin dakai, jikinka yana ta zubar da jini aiy'n bara na kira dactor" Hannuwanta taji ya damƙa tare da girgiza kansa tare da jan numfashi da ƙyar yana faɗin. "No ba buƙatar hakan aiyn sun riga da sun harben sun gama illatamin rayuwa, nasan bazan rayu ba amma kiyi haƙuri zan tafi ba tare dana ga gudan jinana a duniyar nan ba, zan mutu ne da sonku da ƙaunarku duka ku biyun!" ya faɗi yana mata nuni da phone nashi, da sauri ta miƙa may bayan ta cire daga security'n daya sev da sunanta. Cikin wannan ƙarfin halin ya haɗa musu conect shida *AK* da kuma *ZAYD SURAJ* wata magana suka tattauna sosae. Daga haka yana rungume a jikinta ya furta. "Karki bari little kamaal yay kukan maraici ki tsaya masa tamkar yadda uba yake tsayema ƴaƴansa duk da nasan ban tafi nabar baya lusaraba baya jaruma na bariiiii" se kuma ya saki zancen yana ɗaukar kalmar shahada. Zayd suraj ne cikin ƙarajin da yafi kama dana tashin hankali ya shiga furta. "A ahhh!? A aaa kamaal kada ka tafi karkai mana haka Insha Allah ma zaka ga gudan jininka zaka rayu dashi ba zaka barmu ba KAMAAL YOUSUF RANO" Ina sedai har me afkuwa ta riga da ta afku domin kuwa maganar nan ta *kullu nafsin za'ikatul maut* ta tabbata akan wannan bawa nashi wato kamaal Rano. Wani kalan ihu marria ta saki tana faɗawa jikinsa itama nata numfashin na tafiya yana barin jikinta..... Dip dip ƙaran datse kiran da AK yay daga can. Zayd kuwa da suke gari ɗaya a wani kalan mugun guje ya fice duk da yadda dogarawan gidan sarautar suka so hana shi fita, amma kallo ɗaya ya wurga musu suka bashi hanya. Wani kalan gudu na tashin hankali yake tamkar wanda ya samu cutar taɓin hankali don har tashi sama yake, ta inda Allah ma ya temake shi shine cewar dare ne ba rana ba. *BY AMMEYLAYLERH* KUYI HAƘURI!!! _Duka fages ɗin nan uku abubuwane marasa daɗi ke faruwa_ _Dama haka rayuwa take mu sani wani loƙaci kuka, wani lokaci kuma ayi dariya_ _Ba komai akwai dariyan gaba kuma don Allah mutuwan Kamaal karya zama kamar na *ALIYU SHUREIM* ɗin *QUEEN*_ _kudai kawai ku taya marria da adda'an samun lafiya da sauka lafiya_ _kana ina tunanin loƙacin dawowar AK Nigeria yayi da kuma barinta na har abada da zaiyi da sunan aiki, se dai inda ziyara kamar in ya rako matarsa lol😁😀_ *Byeeeee* *🦅 MIKIYA 🦅* _A wonderful world & Special anti terroRism squad_ ____________________ *MARYAM NASEER MIRRAH* ~AMMEY LAYLERH ✍️~ ✯ *~🌠 JAJIRTATTU WRITER'S ASS.... 💫~* BOOK Two…………………………񆬍✍ 39&40 # Hot Romance scene # Real life # Hot love scene # Ak meerah # A.k.a AMMEYLAYLERH👍👉 *Bɪꜱᴍɪʟʟᴀʜɪʀ Rᴀʜᴍᴀɴɪʀ Rᴀʜɪᴍ* ♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡ ★ Cikin ƙanƙanin loƙaci se gashi a gidan kusan tare suka shigo shida jami'an daya ƙira a hanyarsa na zuwa. Tun daga bakin get na gidan suka fara cin karo da gawawwaki. Haka har suka dire ga Kamaal ɗin dake kwance babu rai jikinsa da kuma marria da itan ma dai babu numfashin tattare da ita. Cikin hanzari suka raba marria da jikin Kamaal nan aka tattaresu zuwa asbiti domin duba lafiyarsu duk da cewar sun san kamaal ɗin ya riga da ya mutu. Amma dole a matsayinsa na jami'a a duba ainihin abinda ya faru dashi duk da sun san abinda ya farun ganan halamar hakan. Baki ɗaya su kuma wadan da suke kwance aka kwashe ana zubasu wota motan na daban, baki ɗaya suka tattara bindugun su kamaal ɗin dama na sauran ƴan ta'addar. Bayan isansu hospital duk wani bincike daya danganci case ɗin mutuwar sunyi, kan marria suka koma duk wani taimakon gaggawar daya kamata sun mata amma bata farfaɗo ba. Cikin ƙanƙanin loƙaci ƴan uwan su kamaal daga rano suka cika hospital in tare da gidan shi. Kuka kuyi na ladamar wofan tar dashi da sukai sunyi har ba adadi, Ga kuma halinda marria take cikin na rashin farfaɗowanta, haka suka tattara suka koma ana barin mamanta tare da ita. A gidansa aka may wanka, bayan an sallace gawar kamaal haka aka miƙa shi gidan sa na gaskiya. (Allahu Akbar rayuwar duniyar kenan haka dai- haka dai loƙacin da kake kan ganiyar jin daɗinta, sai kuma mutuwa tazo ta riske ka a yayin da baka yi zata ko tsammani ba. ka shirya ko ba shirya ba taɗauke ka Allah yasa mu yi kyakyawan ƙarshe Ameern ya rabb,Ubangijii yaji ƙan Aliyu shureim) Bayan mutane sun dawo daga maƙabarta haka zaratan matasa suka rinƙa shigowa cikin gidan suna gaisuwar kamaal ciki kuwa harda jami'ai abokan aikinsa. Dsp daya zo haka ya zube gaban kwarya kwaryan cikinsa yana matsan hawayen munafunci. "Allah ya jiƙan kamaal yaron kirki dashi wllh. Kai duk wanda ya kashe wannan yaro Allah dai ya toni asirinsa cikin gaggawa" daga cikin zuciyarsa yag saurin cewa (Yaseen ba ameen ba) lol☺😁 kunji shege mugu fa. Haka akaci gaba da karɓar gaisuwar kamaluddeen bawon Allah, daga ko ina daga ko wacce duniya yabone kawai ke tashi akan kamaludden ɗin, kasancewar shi mutumne shi na mutane babu ruwansa da girman kan nan irin matasan yanzu da suke ɗorama kansu da zafi. Don malam bahaushe kance kowa ya ɗebo da zafi to bakinsa tabbas wannan haka yake. haka dai Kamaal ya ringa shan yabo daga bakunan mutane maban banta, musamman ma talakawan da yake shige musu gaba yayin da wani iftila in ya afka musu. Rayuwa keñan in kayi dakyau kanka haka za inma akasin hakan ne kanka.Kamaal kam Saidai muce alhamdulillah ya sami tarin shedar mutane sai fatar hamdala kammm. Kuka kuwa jama'a da dama sunyi kuka iyaka kuka sosae. Kakarsa iya Inno se kuka take cikin kukan take furta. "Allah ya jiƙanka kamalu kamaludden, mutum me daraja da kamala me halin tattako da ban girma, Allah sarki Allah beyi zan rayu dakai ba kamal amma insha Allah zan rayu da abinda ka bari a duniya kamalu" tayi maganar tana shaftar ruwan hawaye me tafe da majina. ★ Se da marria tai kwana biyar kana ta farfaɗo wannan karan mikin dayay mata tsai arai shine ya fara faɗo mata. Ahankali ta shiga bin ko ina da kallo harta dangana da kallon mum nata dake sallah ta kalli alkibla, Saurin fusge ledan ruwan tayi a jikinta tuni jini ya fara yarara a hannunta data fisge canular dake hannunta. "Ummata ina *YAAYAA KAMAAL NAAAA?* kinsan mafarkin danai ummata?wai a cikin mafarkin se ga wasu ƴan daba suka zo zasu kashemin Aiy'n, Wai shine na dauki bindigar nima na ringa kashesu, amma fa wai shiɗin ya mutu inata kuka kinji mafarki da soko ko umma" Tay maganar tana ta kallon ummanta dake ta sallar kwallan daya riga da ya cika idanun mum marria tasa bayan hannunta ta share don batason marrian taga tana kukan. Miƙewa tayi tana nufar inda marrian take, zama tayi gefen gadon da take zaune ga kuma hannunta na ɗigar jini. Kanta umman ta janwo tana ɗorawa kan ƙafafunta sumar kanta ta soma shafawa a raunace tace "Marria kamaludden kam ya rigamu gidan gaskiya se haƙuri" wani irin kwace jikinta tayi a na ummanta, se kuma ta shiga ja da baya baya tamkar wata sabon kamun hauka. Ummace ta riƙota ganin abinda takeyi cikin tausasa murya ta shiga faɗin. "ki daure!,ki daure, ki nutsu, nutsu Marria ki danni zuciyarki don Allah. Maza nutsu nasan da matuƙar ciyo hakan dole kiji matuƙar ciwo ki kuma fi kowa jin ciwon mutuwar kamaal duba da cewan har yanzun ko shekara baku ƙarasa rufawa da auren kuba. Amma hakan ba shi zai ba ki dama ki mance da cewar ubangijin daya bamu kamaal shi ya karɓi abinsa duk mai rai kuma mamacin. Kana mutuwa dolece a wuyan kowanne ɗan Adam kamaal kam ya riga mu gidan gaskiya Allah ya gafarta masa!, Ubangijii yasa yayi kyakkyawanr ƙarshe yasa aljannatul Firdausi itace makomar kamaludden"Mum marria ta ƙarasa maganar haɗi da goge kwallar data cika idanunta taff na tsananin tausayin ƴar nata. Cikin ɓacewar tunani na ɗan wani loƙaci muryarnta na rawa tace. "ummiey meya faru naga kina kuka"? Daga har nurses dake tsaye akanta babu wanda maganar marrian bata girgiza ba, meya faru fa take tambayar su?. Kenan me hakan ke nufi badai tayi loosing memories nata bane?. Ummanta ce ta janyota jikinta tana ɗora kanta saman ƙirjinta cikin dakewa da shanye ciwon dake sukar ƙirjinta umman ta dubeta tare da cewa. "Marria kamaal mijinkine ya rasu!, ya tafi ya barki yabar gudan jininsa a tare dake ba tare daya ganshi ba, ya tafi yabar kowa da kowa na cikin duniyar ma baki ɗaya saidai Allah Ubangijii yaji ƙan kamaludden domin ya riga mu gidan gaskiya, gatan da zamu masa shine binsa da tarin adda'oinmu!" wani irin murmushi ta saki irin mai ƙona zuciyar nan tace, "kin yarda keñan? dama kema umma ashe kin yarda bakiji me nace miki ba cewa nay miki nayi mafarkin wasu sun shigo gidan mu sunyi harbin bindiga shine suka kashe min yaya kamaal na a cikin baccin nima kuwa duk sena kashesu. Barama ki gani ina wayana take na ƙirashi nace yazo yanzu kuwa zaki ganshi dan ma ki tabbar da cewan a mafarki nake" tayi maganar tana lalubar inda wayanta yake. "Innalillah wa'inna ilaihir raji'un"² Ummanta, nurses,dama Zayd suraj da tun farkon fara sambatunta ya ƙame ƙamm ya kasa shigowa dan ji yay ƙafafunsa sunyi may nauyi. Wani irin matsanancin tausayin marrian na kama shi cikin son gasgata mata kamaal kamm saidai wani ba bashi bane. Zayd suraj ya furta "Kamaal yatafi kamm marria wannan abu da kikeyi bashi zai sa yadawo gareki ba, da ana mutuwa adawo marria da yanzu mun dawo da kamaal cikin wannan duniyar kodan ɗorawa daga inda ya tsaya!, kodan ya ƙona zuciyoyin maƙiyansa sai dai kash wannan kalmar ta *Kulli nafsin za'ikatuol maut* ta jima da hawan kansa. Saidai haƙuri! Adda'a juriya da jajircewa kamar yadda ya ce dake" A tsorace marria ta ɗago dara-dara idanuta masu kaifi ta ɗora akan zayd ɗin, kafin ta shiga girgiza kai hawaye na fita a idonta tace. "A ina ya mutum? Muje ku nuna min, wllh idan na farka daga wannan baccin baran sake komawa ba, sedai naita zama ido biyu.idan kuma da gasken kuke to wllh Nima binsa zanyi idan ya mutu sai muje cenñnn muyi rayuwar aurenmu a maƙabartarma, harda babynmu ma da zamu haifa ai shikenan kooooo Ummata"? Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un kawai suka shiga ambata ganin kamar ma marrian bata a cikin hayyacinta da nutsuwar tane. kallo ɗaya zaka mata kasan cewar Samm bata a hayyacin tane, cigaba tayi da kallon zayd da kuma ummanta ganin kowannensu hawaye yake daukewane daga idanusa, ya sanya sosae tsoro da zallumi haɗi da tashin hankali wanda ba'a sa masa rana na lulluɓeta Wanda tunda take tsawon rayuwarta bata taɓa irskar irin sa ba ya ziyarci zuciya da gangar jikinta, ji tayi wani irin abu yasoma ratsa baki ɗaya ilahirin jikinta . sai kawai jikinta yafara rawa kamar mazari.Cikin muryan da yay ƙasa sosae tace "Shikenan yaya kamaal na yatafi ya barni, ya tafi ba tare da yaga babyn da zan haifa mana ba?, ya tafi ya barni da kewa da maraicin rashinsa? na tabbata nima nayi ban kwana da farin ciki kenan ko?, wallahi umma ba zan iya rayuwa ba tare da Aiy'n ba nima mutuwa zan yi domin ban ga amfani rayuwata ba in ba tare da aiyn ba, kinga ƙara kawai na bishi idan mukaje can sena haifa mana baby'nmu muyi rayuwanmu mu kaɗai ko dan Allah Ummalolona?" se kuma ta fashe da dariya tana soma riƙe cikinta seta fara faɗin "Dan jinjirinmu ai dan Allah Abiey'nka ba ragon namiji bane ko? Kuma babu wanda ya isa harbinsa ma ina nannnnnn........ $e kuma komai ya sake tsaya mata chakkk tana sake sumewa. Fashewa da kuka mum marria tayi tana ta ambatar duk wasu adda'oin da suka zo bakinta tana jijjiga marrian. Cikin ƴan mintuna kaɗan ta kuma farkawa, amma wannan karon kammm ko damar sunbatun bata samu ba, sedai bin kowa da take da rinannun idanun da suka jeme sukay jaaaaaa sosae. Da wani kalan saurin tashin hankali zayd suraj yabar wurin don bazai iya ci gaba sa sauraren zararrun kalmomintaba. Ko kallon gabansa baiyi kai tsaye motansa ya faɗa yana mata key ya kwasheta da wani mugun speed na hauka. Shi kaɗai a zuciyarsa yake raya duk masu sautsayin da Allah yasa ya gano da kwai sakun hannunsa a mutuwar abokinsa babban amininsa kamal Rano, ya rantse shima seya raba shi da nasa numfashin. Yanxu dai dan Allah dubi yacce suke ƙoƙarin haukata matarsa a sanadiyar mutuwar mijinta. Sun maida mishi ɗa ko ƴarsa marayu tun kamin su zoma duniyar da ba komai cikinta banda tarin kunci, hasaada, cin Amana, rashin kishin ƙasa, zanba cikin aminci. Da dai duk wasu abubuwa marasa kyau, to mema mutum zeyi a cikin wannan duniyar kamm uhmmmm? Ya tambayi zuciyarsa hakan. Wani ɓangare na daga cikin zuciyansa yace {babu} Yau kwanaki biyar kenan daya rasa abokinsa kamaal ɗin, kuma tun a daren ranar ya fara gudanar da wasu bincike tare da ƙwararan hujjoji domin gurfanar da mara gaskiya maciya amanar ƙasa da kuma aikinta. ★ Tun daga wannan loƙacin marria ta koma kamar wata zararriya ita kaɗai ka ganta tana dariya wani bin kuma ka ganta tana kuka. Ga kuma wani sabon al'amari daya kunno kai shine na juyewar magana daga yadda gaskiyar lamari yake zuwa ƙarya, wai marria itane ta gayyaci ƴan dabar nan da su kashe mijinta in ba hakaba meye yasa ita ko kwarzane bata jiba? Me yasa ba'a sameta da karzanen ciwo bane. Wannan abu shiya sake rikitar da duk wani makusanci nasu marria, sedai zayd tsaye akan komi tun a daren jiya ma yay magana da AK yace lallai dole akwai buƙatar ya dawo neja. Hakan kuwa akayi a washe garin ranar AK ya dira a nigeria. wanda yay daidai da ranar dasu mah suka miƙa meerah ga sashin AK ɗin. Yana zaune kan wata farar royal coution dake gaban pool nashi na nigeria. Tsaye ya miƙe cikin tsabar tafasan da zuciyansa ke masa hannunsa riƙe da guns. Seti ya dauka tare da harba bindigaf a irin abin gwajin nan. Ta farko seta goce, Kallonsa arms yayi tare da furta "Baka samu ba!" shade dake idonsa ya cire tare da faɗin "Wannan ze samu" ya faɗi yana sake harba ta biyu da uku duk suka harbi tsakiyan paypay ɗin inda suke ya kalla tare da furta. "Gotawar seti sam ba ɗabi'ar *ABDOUL-MALEEK AK* bane. Kamar yadda Ak be kamaci ya zamo abin setin wani ba. Kamar yacce aka wayi hari har wasu sun fara cin dunduniyata" Milea ne y kalla AK din tare sa faɗin, "bara na ɗan zaga Boss" kansa ya jinjina masa tafiya ya fara taku daya ana biyu sejin sauƙar harsashi yay a tsaƙiyar gadon bayansa. A ɗan razane duk suke kallon AK ɗin. "Amma Boss me yasa?" Arms yay tambayar tunda yasan boss ɗin nasu baya taɓa aikata ba daida ba. "Shiga hurumi! Arms duba" ya faɗi yana sake harbin setin kafar miles ɗin. da sauri arms ɗin kuwa ya isa ga miles yana duba ƙasan shoe nashi kamar yacce AK ɗin ya buƙata. A take kuwa se gashi hannunsa rike da plash camare wacce ya dauƙo daga cikin takalmin miles ɗin. Cikin wani kalan taku har wani ɗan rausaya yake ya sake furta. "Kada ka yarda da kowa ka kashe koma waye ka zama naka kai kaɗai.Yare ɗaya ne a duniyar nan wanda kowa yake fahimtarsa, shine kada ka yarda da kowa wannan shine" daga haka ya yasanya kansa yana barin bakin pool ɗin kai tsaye. Kuma Zaid Emaar's yana nan a ƙasar naijan shima. Bedroom nashi ya wuce kai tsaye duk wasu sauran hujjujin da zayd ya kawo mishine ya gama haɗesu wuri guda. A kuma daren ranar yabi jirgi zuwa Kano don a gudanar da shari'an dashi. Xuwa loƙacin kuwa duk wanda yaga marria seya tausaya mata. Don abin a tausaya matace don kuwa kalmar nan ta taɓin hankali na neman tabbatuwa akanta. Wai hakan ma dan tsaye mahaifinta yake akanta ga kuma zayd da kuma jajircewarshi garesu, duk wani nauyi da dawainiya da su ya ɗauke da kansa. A randa kuma ta haihu a ranar Insha Allah za'a sake ɗaura Aurenta a karo na biyu da *ZAYD SURAJ SHUREIM* kuma sunyi na'am da hakan domin kai tsaye roƙo na ƙarshe da Kamaal ɗin ya masa kenan kuma a gaban AK ne se kuma ita marrian, Tunda ta fara dawowa cikin nutsuwanta shiru ya zama shine abokinta, fuskan nan me yawan fara'a da ban dariya duk sun gudu nasu wuri. A loƙacin kuwa da Babanta ya sameta da zancen loƙacin ma wajen wata biyu da rasuwan kamaal ɗin bal tace samm ita bata yarda ba. Ai ita da kuma auren wanin kamaal har gaban abada. Anan kano sukay zaman farko, inda ido da ido suke neman danne gaskiyar abinda ya faru, daga karshe ma zayd se ɓoye iyayen yarin yay a gidansu. Domin barazanar mutuwa da wasu manya keyi dole ya daukaka ƙara zuwa *ABUJA* dan yace Insha Allah seya cikama kamaal muradinsa na amsarwa wadan nan mutane haƙƙinsu. Babu zata mataimakin gwamnan kano yaga sammacin ɗaukaka ƙara zuwa babbar kotu ta gaba shida ɗansa fayel. Nan da kwanaki uku don haka ya shirya shedun ƙarya da kuma manyan mutane domin bashi kariya shida yaronsa kodan kada sunan ya ɓaci da kuma rashin kujerarsa da yake matuƙar ƙauna. Haka dai sukay duk wasu shige da ficensu kuma sunyi ƙoƙarin ganin kota wacce siga sun kwato wannan dayan ƙarshen da marria ta harba, wanda kai tsaye shine ya sanar dasu wadan da suka aikosu su kashe kamaal ɗin har dama matar nashi. A lokacin kuwa da Dsp yaga takardar sammaci na biyu harda ƴar guntuwar gudawarsa yay don kuwa abu ne baiyi zata ba. _A yau ranar Asabar 5/10/2024_ babbar kotun maƙil take da jama'a ta ko ta ina ciki kuwa harda shegaban kasar A..K...K dasu Ak shida Zaid Emaar's amma dun ɓoye fuskokinsu ne cikin mask, duk wani wanda masu gidan rana suka zauna masa daram to kuwa yana a cikin wannan kotu don wanke dan uwansa Hon Iliyasu maitama da yaronsa fayel maitama. "KOOOTU!" Alƙali ya buga ƴar hidimarsa tsittttt kuwa kotun ya dauka. Nan ya umarci da masu kare fayel dasu fara gabatar da shari'ansu. Nan suka shiga zayyano manyan hujjojin karyar da suka tanaja domin kare kansu. Mutum ɗaya ne daga cikin masu kare fayel ya miƙe yana furta. "Ya me girma me shariya kamarrrrrrr" Hhhhhhhhh to muci gaba ko? Amma a fage na gaba. To nake ga mu dakata a nan _Shin zamuga su waye zasuy nasara?_ _Shin Zayd suraj ne zeyi nasara ko kuwa su Hon iliyasu maitamanae da nasarar?_ _Tammm ƙaƙa kara ƙaƙa karfa ku manta yau kam ga AK ga kuma A..K..K shugaban kasar nigeria kenan, wanda yay shijira daga ƙasar sa KUWAIT zuwa tamu ƙasar Shin karku manta dama shine next target na AK_ _Ya kuke gani marria zata auri zayd suraj kuwa?_ _To dai duk mu haɗe a fage na gaba donji yadda zata kaya_ *Alhamudlillah mun taho gangara kuma Insha Allah Aski ya zo daf da goshi. Acikin kashi ɗari munyi kashi Casa'in kunga kuwa ay munzo gangare gangare wow Masha Allah Allah abin godiya* *BY AMMEYLAYLERH* A GIMTSE KOOOO?😁