𝐃 𝐔 𝐍 𝐈 𝐘 𝐀 𝐓 𝐀 ̶B̶O̶O̶K ̶2 ⱧɄ₲Ʉ₥₳ 𝙋𝘼𝙂𝙀 1 𝘼𝙢𝙗𝙞𝙩𝙞𝙤𝙣 & 𝙨𝙪𝙘𝙘𝙚𝙨𝙨 𝙈𝙪𝙝𝙖𝙢𝙢𝙖𝙙 𝙛𝙪'𝙖𝙙 𝙟𝙖𝙙𝙙𝙖 "Hustle until you no longer need to introduce yourself,push your self because no one else is going to do it for you". Kalamansa na qarshe kenan da tarin mayan attajiran da sukayi meeting na qarshe dasu wanda keson saka share dinsu cikin sabon kamfanin da kwanaki bakwai suka rage masa ya budeshi. Kalamai ne da suka dauki hankulan mutanen dake wajen,wanda dasu aka kammala zaman. Sanda yake sallama dash fiye da rabin hankalinsa yana kan wayarsa da tun dazun ya lura tana haske. Sai da gurin ya rage saura shi daya da hudu daga cikin guard dinsa da wannan karon dasu yayi tafiyar wadanda ke nesa da inda yake,ya miqa hannu a nutse yana jawo wayar gami da fesar da iska me dumi daga bakinsa. Cikin kowanne motsi yana jin farinciki na yadda al'amuran bude kamfanin ke gudana da dukkan wani haske qyalli da kuma alamu na nasara,bai taba qwallafa rai akan wani abu kaman haka ba,baisan me yasa dukka tunaninsa da hankalinsa suka raja'a wajen son ganin cikar wannan mafarkin nasa ba. Tunda yazo samu cikakken zama na awa biyu cur ba,saidai idan dare yayi ya wafci wasu awanni ya tilastawa kansa kwanciya ya huta. Kowanne minti idan ya shude da amfaninsa a wajensa,ko baya din dama shi mutum ne me girmama lokaci tare da bashi muhimmanci qwarai. Sunan farouq kawai daya gani ya sakashi gyara zama yana furta "Ya salam" Qasa qasa fuskarsa nason fidda wannan sihirtaccen murmushin nasa da ba kasafai ake samun dacen ganinsa ba. Wani sirri ne kwance cikin murmushinsa dake qara masa haiba da kwarjini da fitar asalin kyan da ubangiji ya huwace masa. Yasan zayasha qorafi ne kawai wajen farouq din......don yace masa zai kirashi har baisan adadi ba......hakanan bazai ma iya tuna awar qarshe da sukayi waya ba. "Hala baka da wani abu me muhimmanci cikin rayuwarka sama da business dinka?" Kalmar da farouq ya fara jera masa kenan. Boyayyen murmushi ya saki yana daga dogayen qafafunsa ya aza saman dunqulallen table din gabansa me azabar kyau. Wani irin shaquwa da fahimtar juna ce tsakaninsu dake sanyasu iya fahimtar mode din juna koda basa kallon fuskokin juna. Yasan zaiji fiye da haka ma a bakin farouq din,don muryarsa a dake take da alama har kan fuskarsa akwai alamu na qosawa "Idan ka cire ku family na.......tabbas ba abinda ya fishi muhimmanci cikin duka kaf rayuwata". "Aurenka da yarinyar su a wanne muhalli ka sakasu?....." Ya sake masa tambayar kansa tsaye cikin salo na kaiwa maqura da son masa titsiye. "Aure?....yarinya?" Ya maimaita maganar har ga Allah cikin son neman qarin haske. "Eheeennn" Farouq ya fada a taqaice,cikin ransa yana jin rainin hankalin jadda yana neman fin qarfin tunaninsa muddin ya gaya masa ya manta da lamarin auren dake gabansa. "Mmtsewww......au" Fuad ya furta wani siririn murmushi yana sake qwace masa. Sai a yanzun kwanyar tayo masa tariyar karatun baya na abinda ya baro a nigeria. Kusan gaba daya sabgar ta shafe daga tunaninsa,abinda ya sanya a gaba ya mamaye tunanin komai daga kansa. "Am sorry......kasan halin......" "......halin mijin aljana.......zata sakashi ya aikata fiye da haka ma,saidai alhmdlh.....duk abinta a wannan karon munci qarfinta,kuma in sha Allah dan uwana bazai mutu babu aure ba". Dariya sosai ta qwace ma fu'ad din ganin yadda farouq din ke maganar very serious,abinda ya jima baiyi ba,ya rasa abinda yasa suka damu da auren nan......ya fuskanci gaba dayansu murna suke dashi.....ya karanci dukkaninsu sun daukeshi serious kuma da gaske suke lamuran baki daya.....ciki harda MAAMAH duk da akwai qatotuwar ayar tambaya a kanta......don ya sani,koda yaushe ita ungulu bata jewar banza. "Ka duba email dinka na sauke maka saqo......ka duba urgently" "Alright" Ya amsa masa suna katse wayar dukansu. Yasan tsaf xaya iya mancewa idan bai duba saqon yanzu ba kaman yadda farouq ya buqata. Don haka kanshi tsaye ya bude email dinsa. Baibi takan sabbin saqonni da ya fahimta kaman akwaisu ba,kanshi tsaye ya bude saqon farouq din. Daya bayan daya yake bin hotunan daya turo da kallo ba don yana fahimta can can ba. Hotuna ne na style readymade na kayan maza masu azabar kyau da aji da wani fitaccen kamfanin fidda readymade suturu ke samarwa. Company ne da sanya suturar data fits daga cikinsa sai wane da wane......sai mutanen da suka amsa sunan shegu ne su ta fannin kudi da dukiya. A idanu kayan sunyi kyau,saidai shi baisan me zaiyi dasu ba,don haka ya jawo daya wayar tashi ba tare daya dauke dubansa daga kan hotunan kayan ba ya dannawa farouq din kira. "Am coming" Abinda yaji farouq din ya fara fadi kenan da alama yana magana da wasu ne daga gefe "Have you seen it?" Idanunsa ya lumshe kadan sannan ya budesu "Yes I have.....but bansan me zanyi dasu ba......hala ka fara preparation na bude garment company ne?". Wani qululun takaici ya tsayewa farouq a wuya,seriously mutumin nan da gasken gaske yake ya fara mantawa da cewa aure zaiyi. Duka ya sakar masa ragamar komai a hannunsa ba tare da damuwa ko tambayar ya ake ciki ba ko meke faruwa ba. "Na rantse da Allah sa'arka daya baka kusa dani......shin wai ka manta yarinyar mutane da zaka aura wadda ka kaiwa sadaki?,in all likelihood ka samu memory formation right?" . Wannan karon ma saida sautin dariyarsa ya isa har kunnen farouq ''Calmdown mana dude......abun yayi zafi ne har haka?" "Yama fi haka zafi" Ya fada yana jin ya tuqewa halin fu'ad din. "To am sorry......amma dai ka sani......ina da abubuwa masu muhimmanci da yawa a gabana.....kai din kuma wakili nane a ko ina......duk abinda ya dace ka zartar ka zartar....na baka wuqa da nama" Ya fada calmly,don bayason ya sake tunzura farouq din,tunda yana ganin yana iya bakin qoqarinsa a abinda shi a nasa ganin baikai muhimmanci da suke bashi ba. Dan shurun da farouq din yayi da yadda ya sauke numfashi ya tabbatar masa fushinsa ya sauka,dama ko can basa wani dogon fushi da juna,da farouq ya zazzage abinda ke cikinsa shikenan,shine dama me yawan kauda kai.....zaka jima kana masa abu amma miskilancinsa bai bari ya nuna maka har kasan kana masa ba daidai ba,har sai sanda ya gama taraka tukunna. "Kayi magana dasu abdulghafar......for now ya kamata su sassauta tsaronsu akan yarinyar" "For what reason?" Fu'ad ya maida masa kanshi tsaye yana gyara zamansa sosai saman lallausar kujerar da yake zaune akai. "Ina ganin kaman ya kamata ta sake.....duk da dama dole ka bata security da guard,ko don yanayin halin tsaro da qasar ke ciki,sannan zuwa yanzu ta zama part of us......wanda duk xai d'amfara da sunanmu dole a bashi tsaro" "Forget about it farouq......she's gonna be able to do what you....." Sai kuma ya fasa qarasawa yana jan siririn tsaki. Shi sam sam koda sau daya bai taba jin wani abu da yayi kama da yarda ko gasgata yarinyar ba.....akwai abubuwa da yawa da uake suspecting a kanta,wanda ya sake qaruwa tun daga lokacin data bayyanar masa a mazaunin ZABIN MAAMAH. "Do you have concern about her actions?" Farouq ya tambayeshi yana tattara masa hankalinsa. "Manta kawai......mu ajiye wannan,baka tambayeni akan komai ba dude?". Yayi maganar calmly kaman zancan business din yafi bashi peace akan batun auren. "Akan komai?,akan business dinka?,wannan shine kadai damuwarka?" "Wani abu daban daya kamata na damu dashi sama da haka?". Numfashi sosai farouq yaja,yana tsoron yadda fu'ad gaba daya baya bawa harkar nan muhimmanci,yana tsoron faruwar wani abu......careless din yayi yawa har haka,yana jin kamar ya kashe wayar kawai,to amma ya sani wannan shine abu na qarshe da zaiwa fu'ad ya bata masa rai,ya tsani a kashe masa waya sam sam. Yadda yake masa bayanin nasarorin da sauran abinda ya rage ya sake bashi tabbacin business dinsa shine gaba da komai. Sunyi magana har ta kusan awa guda kafin su yanke sadarwar dake tsakaninsu. Sanda yake qoqarin minimizing email din idanunsa suka sauka kan wani sabon adreshin email din dake dauke da sabbin saqonni guda uku,kamar zai share ya wuce sai baiyi hakan ba,ya danna ya budeshi ya fara bin saqonni da kallo. 𝐃 𝐔 𝐍 𝐈 𝐘 𝐀 𝐓 𝐀 ̶B̶O̶O̶K ̶2 ⱧɄ₲Ʉ₥₳ 𝙋𝘼𝙂𝙀 2 Kallon farko zaka fahimci ya bada dukka hankalinsa akan abinda yake ganin gilmawarsa cikin wayar tasa. Saqonni ne kusan guda uku,kala daban daban,saidai kuma kowanne saqo daya yakeson isar masa. _mr muhammad jadda,You hereby warned to stop all activities related to lunching your company_ saqon farko kenan. A nutse ya sauke idonsa zuwa ga email na biyu _Not heeding this warning may put your personal and professional assets at risk_ . Sake matsawa yayi zuwa saqo na uku shima still dai kakkaifan jan kunne ne zalla a cikinsa. _Ignoring this warning may lead to financial losses and reputational damage_ still dai qasansa shima wani saqonne _Proceed with caution,as this may have unintended consequences_. Tsam yayi da ransa,yana sake bin saqonnin daki daki yana bitarsu. Wannan wanne irin barazana ce haka me girma?,daga wanne sashe ta bullo?,su waye keda alhakin aiwatar da hakan?. Ya jima da sani......ba sanin jiya ko kuma yau ba.....sana'arshi sana'a ce dake dauke da tarin hamayya gogayya da kuma abokan adawa na sarari dana boye,wani irin matsayi ne da Allah ya bashi wanda bai taba tunanin samuwarsa a qananun shekaru irin nashi ba. Akwai tarin mutanen da suka fishi jimawa cikin harkar.....saidai har yanzu basu samu irin nasibin daya samu ba. Gyara zamansa ya sakeyi da kyau yana furzar da iska daga bakinsa. Ya sani,zai iya bincike akan ainihin adreshin,saidai kuma yasan zai wahala ya iya reaching komai akai koda yaso samun haka. Beside ma,isn't the first time daya fara samun ire iren wadannan saqonnin,wanda daga qarshe yake cimma daga wanne waje suke?. Ba abinda ya taba girgizashi ko ya daga masa hankali kwata kwata,amma kuma hakanan yaji wannan saqon ya tsaye masa a rai. Bai sani ba.....ko don saqon yazo masa ne a daidai sanda yake da burin aiwatar da abinda ya qwallafawa ransa na cikar burinsa?. Yadda yake a tsaye a siffa da zati me taba zuciya,haka zuciyarsa take a tsaye. Ba komai ke bashi tsoro ko firgitashi ko sanyashi yaja baya akan abinda ya fuskanta ya kuma qudira zai aiwatar ba.....don haka wannan saqon ma sai ya sanyashi cikin sahun sauran saqonni marasa muhimmanci,wadanda ba komai bane a ciki face zallar barazana maras muhimmanci a wajensa. "Hasbiyallahu wa ni'imal wakil,hasbiyallahu la'ilaha illahuwa alaihi tawakkaltu wa huwa rabbul arshil azeem" Ya furta a nutse,take taji zuciyarsa tana sake samun nutsuwa da aminci. Komai ya tattare yana duba lokaci,cikin jikinsa yake jin ya gaji,yana buqatar cikakken hutu kafin gobe,so samu yabar qasar nan da kwanaki biyar,to amma ya fahimci zai wahala dama ta bashi hakan. Sanda suke takawa da guard dinsa zuwa mazaunin motocinsa guda biyu kira ya shigo wayarsa. A gajiye ya zura hannunsa a side pocket dinsa ya zaluqota. Taku biyu baya sukayi dukkaninsu,wanda wannan kuma sabonsu ne,don basu tsaiwa a waje muddin zai amsa waya,saidai idan shine ya buqaci hakan. Sosai ya zubawa sunan ido yana kallonsa,yayin da zuciyarsa ta cika da wasi wasi da saqe saqen abinda kunnuwansa zasu iya jiye masa daga bakinta. Yaci gaba da irga bugawar da wayar keyi,wanda yake jinsa kamar daidai da bugawar numfashinsa. Ko a tarihi,ko kuma a labari yana kyautata zaton shi din yana cikin mutane sahun farko da idan labarinsu zai fita a kundin littafin al'ajabi zai ja hankalin mutane da dama. Kiran uwa na daya daga cikin kiran dake sanya dukkanin yaro alfahari.......kiran uwa na daga cikin kiran da kowanne yaro ke fatan gani a kowacce rana.....kiran uwa kira ne dake iya juya zuciyar kowanne yaro daga baqinciki zuwa farinciki.....amma banda su......banda tasu mahaifiyar......banda kuma nasu kiran wanda ba komai a cikinsa face zallar ko kwanto da didibniya tsakanin lalubo alkhairi ko sharrinsa. Yana daga cikin motor qafafunsa suna waje ya zauna,yana qoqarin lalubo nutsuwarsa da yakan rasa a duk sanda kiranta ya riskeshi ya daga wayar. Alamun daga kiran ya sanyata sake hada nutsuwarta waje daya,gami da dagawa hajja furaira hannu wadda ke lissafo mata tsare tsare na abubuwan da suka shirya gudanarwa a wata shimfidaddiyar farar takarda. Tsit wajen yayi,bakajin motsin komai da kowa,abinda zai sanya wanda ke nesa irin fu'ad din xaya dauka ita kadai ce wanze a dakin. "Barka da warhaka" Ya furta da muryar nan tasa dake da tasirin kwarjini me yawa da haiba a ciki. "Barka kade.....ina fata kana lafiya?" Ta masa tambayar data zamo abu mafi dadewa baiji ba daga bakinta. Duk da zuciyarsa ta kasa yarda haka siddan tayi kiransa amma ya hadiye wannan.....ko yaya yaji dadin tambayar cikin ransa koda kuwa da manufa aka yita "Alhamdulillah.....Allah yasa kuma hakan" Dan murmushi ta saki,zuciyarta tana ayyano nesanta zuwa kusa da ita. "Lafiyarmu qalau,sai shirye shirye da muke yi gadan gadan". Bai wani fahimci shirye shiryen da take magana a kansu tashin farko ba......har sai data dora da nata bayanin. " Na kiraka ne don na shaida maka.....ina buqatar wasu kudade da zan qarasa duk hidimomin da suka ragen.....ta bangaranka da kuma bangaren ita kanta amaryarka......don kasan hidimar biki ba qaramin abu bane,......bare ni da zan aurar da dan fari......kuma ita kanta yarinyar ya kamata ace ita,danginta da dukkan wani dage da jibi da ita yasan cewa tabbas da gaske mamallakin diamond company zata aura.......banason harkar qaranta......ya kamata duniya kanta ta shaida d'ana zaiyi auren fari". Kusan koda yaushe fitar kalmomin bakinta suna zame masa tamkar makaranta ne......ya jima da sanin maamah din macace me son izza da nuna isa.......ya dauka wani tsohuwar dabi'a ce a tattare da ita.....amma xuwa yanzun ya sake amanna mutuwa ce kadai zata iya samun nasarar rabata da wannan halin. "Me ake buqata?" Ya tambayeta kai tsaye.....don shima da nashi plan din. Zuwa yanzu yana kallon komai ne tamkar a tafin hannunsa ake shiryashi,abinda ya rage masa ya sani kuma kadanne da bayajin zai zame masa me wahalar riska. "Kudi nakeso ka sakamin......sannan ka sakawa amaryarka......kamar million......." "Kiwa saddiq magana......zan gaya masa ya saka miki adadin abinda kike buqata" Ya yanke bayanin da taso yi masa da adadin kudaden da duk da yasan ya jima da fin qarfinsu........amma kuma ana nemansu ne a muhalli da gurbin da babu buqatar yawan wannan adadin. Murmushi ta saki tana jin wani dadi yana ratsa zuciyarta,tun a yanzu tana sake samun tabbacin nasarar dake bibiyarta,tana kuma fara jin qamshi da dadin da uwa keji a yayin da take gwada girman izzarta akan yaranta suke kuma bibiyarta sau da qafa akan duk wani buri ko quduri nata "Allah yayi maka albarka" Ta fada tana murmushi. Kalmar ta dinga masa amsa kuwwa cikin kunnuwansa,sai ya dinga jin kamar ba daga bakin maamah ta fito ba. Idan yace bazai iya tuna ranar data fadi wannan kalmar a kansa baiyi qarya ba. A hankali sai yaji kaman zuciyarsa tana rugujewa. Inama ace ta fadi kalmar ne domin cancanta da kamatar ta fadeta a kansa?,bawai don duniya ko wani abu dake cikinta ba?,bawai don son rai ko biyan buqatar rai ba. Da wannan murmushin dake sake yalwata saman fuskarta a kowacce rana ta ajjiye wayar saman table din gabanta. Qasaitaccen table ne da yazo cikin set na kayan furniture din da aka qawata sabon gidan nata data riga kowa tarewa a ciki. Gida ne datake jin zata kece biki na alfarma a ciki......zata daga sunanta da kuma martabarta a idanun qewaye dama duniya gaba daya. "Kowanne motsinsa sai ya dangantani da saddiq hamza kibiya" Ta fadi tana duban idanun hajja,har cikin ranta tana jin wata wuta tana ruruwa tare dason gaggautowar ranar da zata saka kakkaifar wuqarta ta yanke wannan alaqar da tafi mata kama da baqar alaqa. "Hanzarin na mene mariya?,saurin me kikeyi ne?,saura kwanaki nawa duka duka?" Hajja ta bata qwarin gwiwa tana cike da kwadayi da son jin abinda ya faru tsakaninta da fuad din. Kai maamah din ta jinjina tana son dawo da walwalarta kaman daxun. "Bai tsaya jin koma nawa nake buqata ba......kawai yace nayi magana da saddiq,shima zai masa magana na karbi abinda zan karba din......kinga zan karbi kaso biyu kenan......da nawa dana yarinyar can,zan san mata wani abu a ciki ne kawai.....sai na cire abinda zan cira a ciki.......zan ware na boka donshi kansa yawan kudin dana qara masa akan wanda ya buqata na fahimci ya qara masa azamar aikin nan.....hajja" Ta qarash da kiran sunanta da wani irin sauti dake nuna gajiya da zallar zaquwa. "Inaso yayimin aiki irin aikin da bai taba yin irinsa ba tunda ya fara harkan nan......inason yayimin kalar aikin da ba fuad ba......ko tsuntsun gidan fu'ad sai ya zama me biyayya a gareni........inason yayimin aikin da sabreena zata koma tamkar bawa da ubangidansa a hannuna........bansan me yasa yarinyar ke yimin kwarjini ba,bansan me yasa nakeji wani abu daban ba idan ta kalleni......inason dukka wadannan abubuwan su shafe daga idanuna". Wani murmushi dake dauke da tarin boyayyun ma'anoni da rufaffun qudurori dake amsa kuwwa da amon nawa burin yana sama da naki hajja tayi,sannan ta harde qafarta tana cewa. "Dukka wannan qanqanin aiki ne a wajensa,kuma ko iya haka aka tsaya zaki bawa wani labarin zafin aikinsa......isassun mata kawai ke iya aiki dashi,matan manya da iyayen manyan mutane irinki,saboda daga sadakin aikinsa kawai zaki fahimci ba gama garin boka bane.....don haka ki rubuta ki ajjiye.....dukkanin wadannan burirrika naki tamkar sun gama cika ne......saidai banji share dita a wannan kasafin naki ba". Rausayar da kai maamah tayi tana sakin murmushin jin dadi. A qasan ranta tana mamakin son kudi tsantsa irin na hajja din,duk kuwa da cewa lullube take cikin wadata me tarin yawa.......saidai wadatar yaranta idan kaf idan aka hadesu batakai kaso daya cikin ukun abinda fuad ya mallaka ba shi kadai......amman duk da hakan bata raina kudi komai qanqantarsu(tabbacin zuciya ta zarme da yawa dason abun duniya,Allah ka kiyashemu). "Baki da dukkan wata damuwa hajja,kina da million uku a ciki,kafin alqalami ne kawai......kuma somin tabi,nan gaba kadan ke zaki dinga bada wannan adadin a matsayin taki kyautar" "Qwarai da gaske kuwa mariya" Hajjan ta fada kanta tsaye tana duban idanun maamah da wani irin confidence daya sanya maida hankalin maama duka a kanta. Wannan ya sanya ta sassauta kaifafa harshenta da nuna dukkanin qwarin gwiwar dake kan fuskarta. "Yaronki ai yarona ne mariya...ni nasan bani da haufi....ba zaki taba butulcemin ba" Ta sake yiwa kalamanta ado da wasu kalmomin "In sha Allahu" Maamah ta amsa tana rausayar dakai har yanzu murmushin na saman fuskarta,ta kuma jawo wayarta tana fadin "Bari na nemi musaddiq ya nemo yaron can,don da zafi zafi ake dukan qarfe......gobe nakeso muyi sammakon tafiya hado dukka ayyukan dama sauran bayanai......bikin nan da gaske tahowa yakeyi,kwana shida kacal ya rage......inason tasan da zaman kowacce doka qa'ida dama sharadi kafin ta samu lasisin karbar igiyoyin auren d'ana a kanta". Da wani kallo hajja ta bita kawai ba tare da tace komai ba.....saidai kuma can cikin wani saqo na zuciyar magana ce me yawa nauyi da kuma dogon xangon da bazai yiwu baki ya furtata ba. 𝐃 𝐔 𝐍 𝐈 𝐘 𝐀 𝐓 𝐀 𝘡𝘢𝘧𝘢𝘧𝘢𝘣𝘪𝘺𝘢𝘳 ̶B̶O̶O̶K ̶2 ⱧɄ₲Ʉ₥₳ 𝙋𝘼𝙂𝙀 4 A nutse ta daga kai tana kallon hajjan "Na tsani matsala ko akasi hajja......musamman a wannan matsayin da nake kai a yanzu......me zanyi da ita ballantana na buqaci sharhi a kanta?,bana buqatar dukkan wani jawabi da zai alamta min FADUWA ko MATSALA akan cikar burina a yanzu.......inaji a jikina da raina cewa......zan iya kauda kowacce matsala da zata tunkaro muddin na samu nasarar tsallake wannan matakin da muke kai a yanzu......da qwanjina....da kuma fikirata". Jinjina kai kawai hajja keyi.......tanason taji wanne tanadi da tsari tayi akan hakan?,amma kuma bataso ta zafafa tambaya akai har maamah ta zargi wani abun,saita tattarewa ranta komai tana jiran lokaci.....domin kuwa ta san cewa qwace goruba a hannun kuturu ba abu bane me wahala ba. ********Abune sananne a wajen kowa......sharar biki da yawan maganarsa a bakunan mutanen mu ya ta'allaqa da suna da sharar iyali dangi ko zuri'ar da za'a gudanar da bikin diyoyinsu. Hakan itace ta kasance akan MUHAMMAD FU'AD JADDA mamallakin JADDA DIAMONDCHORE RESOURCES. Daga qishin qishin zuwa samun tabbacin tasowar maganar aurensa,wanda tabbacin ya samu ne daga yadda farouq musaddiq saddiq da uban family alhaji hamza kibiya sukewa bikin shiri na gasken gaske. Daga abokansu saddiq maganan ya fara yaduwa,kafin kace meye wannan labarin ya fara kewaye kowacce kafar sada zumunta. Duk da a qurataccen lokaci labarin ya fasu.....to amma labari ne me dumin gaske daya bawa mutane da dama mamaki.......ya girgiza zukata da zuciyoyin 'yammata da dama......musamman yaran masu kudin da suke kwana su tashi da mutuwar sonshi......suke kuma da qaqqarfan hope din samun shiga a wajensa kodon matsayi da mahaifansu ke dashi......walau na dukiya ko na siyasa......ko kuma kasancewarsu abokan kasuwancin gold da diamond dinsa. A gefe guda kuma wajen 'yammatan da suka hada duk wata sura kyau da isa.....wadanda sukasan basu da wani tsanin isa zuwa gareshi......saidai sunyi mutuwar murus akan mayatacciyar soyayyarsa......abun ya sake bude musu topic of discussion......qarqashin kowanne posting na labarin bikin dake dauke da qawataccen IV na bikinsa da aka qawata da zallar ruwan gold,yake kuma wani irin sheqi da daukan idanun da zai gaya maka bikin ba na yaro bane......tarin cincirindon comments ne da mabanbantan kalamai masu yawan gaske. Da yawansu suna fatan inama zasu samu hotunan amaryar?,ina free wedding pics da sauransu,saidai ko daya basu samu ba face kunji kunji da shaidar zur daga wasu daga cikin commentators na qarya,sai luguden labba da tsabar kyan IV din bikin da aka kashesu dashi.......sai videos na lefen da aka samu wadda ta qwarewa gulma da munafurci ta ba bajesu dashi......abinda ya sake hura wutar tattaunawar. Sam wadanda ake abin dominsu basusan anayi bama......daga angon har amaryar ba ma'abota social media bane........idan kaga ta qulla abota da waya to akwai sabon mission a gabanta........data gama ta ajiye wayar dama layukan da tayi aikin dasu,wani ta karya ta zubar.......wani kuma sai bayan wani zamanin.......yayin da oga fu'ad sam sam ayyukansa basa ma bashi damar tunawa da wani media......koda WhatsApp dinsa idan ka ganshi akai wani abune ya kama da lallai yake da buqatar hawa yayi a can din. Koda yana free ma ko yana annual leave dinsa.......yanayin tsaro da dukka rayuwarsa ke buqata ya sanya ya sake nesa nesa da duk wani harkoki irin wadannan......don komai nasa a matakin rayuwar daya taka yanzu yana buqatar privacy. A daren da ya rage ayyuka sosai......abu daya tak ya rage masa ya kammala yabar qasar. Yana zaune saman bean bag chair,daga gefansa ruwan wolfberry ne me dumi yake sipping yana kuma chewing berries din idan sun shigo bakinsa. Haka kawai yayi shaawar shiga yaga me duniya ke ciki don duka schedule dinsa na yau ya kammalasu. Da wani personal account yake amfani,wanda bai taba ba baya kuma wallafa komai a ciki bare ka iya gano waye mamallakinsa. Akwai account na company dinsa kala daban daban dake qarqashin kulawar ma'aikatansu dake kula da wannan fannin,so amma ko su baya bi ta kansu tunda yayi imanin zasuyi handling dinsa ya dace da abubuwan da ya kamata ace an sanya din. "Ya salam" Ya fada yana miqewa daga relaxing din da yayi cikin bean bag din yana kallon yadda hotunan katinan daurin auren ke shawagi cikin media. Da farko ma bai fahimta ba,saidai daga bisani da suka yita jeho masa ire iren posting din.....kamar sunayi da gayya sunsan shike da alhakin abun har sai da hankalinsa yakai. Shuru yayi yana sauka gami da furzar da iska daga bakinsa. Yasan aikin mutum uku ne wannan farouq saddiq da musaddiq,sai amna ta hudunsu. Kamar jira akeyi ya gani kira ya shigo masa,a nutse ya jawo yana dubawa......farouq ne,kusan tun randa yace ya zaba kaya bai sake barin wayarsa yadda za'a sameshi ba sai yau,sai ya katse kiran,ya koma ya laluboshi video call. Ta signal ya shiga,amintaccen app din da mafi yawan manyan mutane ke ta'ammali dashi saboda samun cikakken tsaro. Shigan farko ya daga,fuskarsa ta fito tarwai kaman yana gabansa. "Hey...." Ya fada qasa qasa yana duban fu'ad "Don't tell me baka ma taso ba?" Yayi masa tambayar yana tsuke fuska tare da bata fara'ar fuskarsa "Zuwa ina kuma dude?.....bakaga abinda kuka jawo ba?,baka ga abinda ke trending ba?" Ya masa tambayar shima hana dan bata fuska kadan. Kai farouq ya jujjuya hagu da dama yana yarfar da hannu "Am asking you seriously fa.....where are you?" "Ask media users......farouq,you take it very serious fa.....wannan fa auren ba wani abu bane da za'a damu dashi har haka ba.....ba wani babban abu bane da zai zama ya yada ko ina ba......it's just a temporary......." "Kai kasan wannan......mu bamu sanshi ba......in fact ma idan ka matsa da yawa zan fiddo komai.....just ka dauko hanya gobe kawai......if not,bazan gaya maka abinda zai faru ba". Datse kiran farouq din yayi,abinda ya sanya fu'ad sakin murmushi ba tare daya motsa daga inda yake ba. Da alama farouq din a qufule yake dashi sosai,shi yasa yayi masa abinda yafi tsana kashe masa kira. Ya kasa fahimtarsa ne,shi sam baiga me yasa zai damu da abinda baida wani muhimmanci ba,baiga abun daurawa kai hidima har haka ba......already sun gama diban kudin komai da komai uban da 'yar,daurin aure kuwa ko aike yayi cikin ma'aikatansa za'a daurashi,gidan da zai ajeta ko ba yanzun ba zai iya bada umarnin tarewarta idan ya gama sabgogin gabanshi,for god sake zai bata lokacinsa ne da ranshi akai?. Bai sake bi takan farouq ba don yasan fushinsu da juna ba wani abu bane me dorewa ba. Saidai yadda farouq din yace idan bai dawo ba washegari baisan me zaya faru ba,yana tsaka da ayyukansa da yake sanya ran sune na qarshe kiran anni ya sameshi. Abdul_haleem daya daya cikin guard dinsa ya miqawa folder din hannunsa,ya koma gefan table din da yake ajiyar takardun ya zauna yana daga wayar. Cikin nutsuwar nan tata da ko yaushe take qara mata kima da kwarjini tayi masa sallama cikin tsantsar kulawa da qauna irin ta uwa da d'a. Kaman ko yaushe shima,cikin tausasawa da matuqar bada kima ya amsa mata sallamar. "Barka da warhaka anni......anni ayyuka sun sani gaba,ayimin afuwa" Yayi riga malam masallaci wajen fada. Murmushi ta saki cikin nutsuwa tace "Anyi maka Muhammadu........ya aikin?,fatan komai yana tafiya daidai?" "Alhamdulillah anni.....komai alhamdulillah,saidai muna buqatar qarin addu'a" Ya furta maganar jerin saqonnin daya gani shekaran jiya suna fado masa. Ba'a raina kaidin maqiyi,kuma abokin adawa ko wanda bai sonka ba'a rainashi komai qanqantarsa. "Kullum a cikinta muke,ba abinda zai faru in sha Allah sai alkhairi......amma nayi zaton samun baquncinka a yau......tuntuni mun sauka a sabon gida.....duka duka jibi ne daurin auren nan......ga baqi a gidan kowa kai yake tambaya". Hannu ya sanya ya shafi sumarsa,har yanzu ya gaza gano abinda yasa suka daukaki sabgar nan haka.....har wani taron gayyar jama'a anni itama tayi kenan bayan ta maamah?. "Jibi din zan shigo in sha Allah anni" "Anni jibi yayi kusa.....gobe ko yau ya kamata....private jet ne,baida buqatar samun wani issue ko ya kawo excuse" Ya jiyo muryar farouq daga gefe tana shigo masa. Murmushi ya saki da sautinsa ya gaza boyuwa,wato zuwa yayi ya hadashi da anni kenan?. "Bani shi anni please" Ya fada da sauri,bata ce komai ba ta miqawa farouq wayar tana murmushi. Drama din fu'ad da farouq babu me shiga,idanma kace zaka shiga din kunya zakaji. "Definitely idan ka samu dama saika shiga tsakanina da anni......ka canza hali wallahi" Ya fada yana dan daure murya. "Kome zaka fada ka fada.....ina nan ina jiranka" "Kaci gaba da jira.....at last idan bakayi wasa ba kai zan daurawa auren nan da yarinyar......tunda naga ka damu da lamarin ta da yawa" Daga haka ya katse kiran yana dariya ciki ciki. Yasan ya kunno farouq din,don ba wanda zai rabashi da fannah dinsa sai Allah. Haka kawai ya samu kansa dason cika alqawarin daya yiwa anni,ya maida hankalinsa qwarai kan qoqarin kammala abubuwan da suke gabansa don ya samu isa nigeria kaman yadda ya alqawarta. Hannu anni ta miqa tana karbar wayarta daga wajen farouq dake mita. Duk da mitar da yakeyi din saidai ya kiyaye dukkan wani abu da zai saka anni ta fahimci akwai lauje cikin nadi.....boyayyen manufa da qudurin data hana fu'ad damuwa da dukkan wani lamari daya shafi auren. "Anni kina sauqaqa masa da yawa........hatta da friends dinmu gobe zasu iso.....amma ace shi yana can neman kudi?.....har yau ya kasa sanin kalmar hutu a rayuwarsa?.....ta yaya zai kula da diyar mutane?" Murmushi anni ta sake,yadda farouq din keta mita ke bata dariya "Banda abinka farouq.....na tabbatar ya fika damuwan ya iso fa.....sannan tunda kaga haka din ba yadda zai taho dinne,da yau gobe da jibin dukka na Allah ne,kuma kaman yau ne.......ina da saqo ma da nakeson ka miqawa d'iyata...." Anni ta fada tana yunqurawa ta miqe. "Ina amna ta shiga ne?" Farouq ya tambayi anni dake qoqarin bude wani side na wata qawatacciyar cupboard ta daban dake cikin aljannar duniyar bedroom din nata. "Tana bangaren beauty spa" 𝘿𝙪𝙣𝙞𝙮𝙖 𝙩𝙖 𝙣𝙖 𝙠𝙪𝙙𝙞 𝙣𝙚. 08187255862 𝐃 𝐔 𝐍 𝐈 𝐘 𝐀 𝐓 𝐀 𝘡𝘢𝘧𝘢𝘧𝘢𝘣𝘪𝘺𝘢𝘳 ̶B̶O̶O̶K ̶2 ⱧɄ₲Ʉ₥₳ 𝙋𝘼𝙂𝙀 5 "Okay" Ya fadi kawai a taqaice,don ita kanta yadda yaga alamun ta dauki bikin kamar yafi yadda kowa a gidan ya dauka. ******A duk bugawar daqiqa,wucewar kowacce saa da kuma bugawar agogo sake kusantar da ita kawai yakeyi zuwa ga duniyar mamakin abinda ke shirin faruwa da ita. Sannu sannu taga gidan ya fara cika da baqin fuskokin da da yawansu ta manta da kasancewarsu ahalinta. Wasunsu tun ana taron alhinin rasa mahaifinsu mamallakin gidan gaba daya,yau sai gasu da daya da daya suna bullowa da sunan halarta taron bikin da tayi imanin ba wani bane ya gayyacesu. Dondai mamma bahijja ba wata mu'amala ke tsakaninsu ba,hasalima ba sanin kaso casa'in da tara a cikinsu tayi ba. Ba sanin jiya ko yau ta yiwa duniya ba,ta sani....kusan mafi rinjaye a cikinsu sanin waye yake shirin aurenta shi ya kawosu bikin,bikin da babu wani abu guda daya da take da masaniyar ita ko mamma bahijja ta tsarayi,koda an tsara din ta tabbatar aikin kawu rufa'i ne,wanda ya kasa zaune ya kasa tsaye,komai yana gaba gaba a kai,hakanan ya saki kudi anata hidima cikin gidan. Yanayin yadda ya saki bakin aljihunsa ya dasawa sabreen qaqqarfan yaqinin kudade ya samu ko ya karba daga wajen mutanen daya sadaukarwa da ita. Bata cewa da kowa komai ba,amma tana karance da kowanne motsi na cikin gidan. Yadda bibo tayi uwa tayi makarbiya,a rana takan hauro saman da zummar dubasu har babu adadi,saman da a baya sai da akasha dambarwa da ita kafin ta daga qafan kasancewarta a can,sai da sukayi baram baram da kawun,ya wanke mata zanin mutuncinta tas tare da buga mata gori nau'i daban daban,yau din sai gata tana zarya tsakanin hidimar da ba tata ba bata kuma shafeta ba. Sanye take da wata simple dubai gown me rangeamen nauyi da sassauqan ado me daukan hankali,cotton ce me yankakken hannu da ya tsaya iya damtsenta,sai siririn mayafinta data maidashi tamkar dankwali ta yane sassalkan gashinta dake zube gadon bayanta ba tare data daureshi da komai ba. Cikin jikinta sam babu qwari,tana jin kamar iska zata iya dibanta ta kayas da ita,hakan kuwa ta sani baya rasa nasaba da qauracewa abinci da tayi akan yadda ta saba cin abinci,duk da dama can ita din ba ma'abociyar cin abincin bace. Ta samu huda ta dafa shinkafa da wake,sai miya da soyayyen kifi daban. Goshinta ta dafe tana zama,kanta tun jiya yake sara mata bayan data jiyo mamma bahijja na magana da qannen mahaifiyarta da kuma kawu Abdul Hakeem,tana shaida masa jibi gobe kenan shine ranar daurin aurenta bayan sallar juma'a. "A zuba miki adda?" Huda ta tambayeta cike da fatan ta amsa cewa zataci din. Hannuwan huda da sukasha lalle tabi da kallo. Ko nata hannuwan farare suke sidik da zara zaran yatsunta dake dauke da dan baqin lalle dan kadan saman farcenta,ragowar lallen data yiwa adon yatsunta wata biyu baya da suka shude. "Zuba......amma kada kisa miya.....mai zaki saka da dan maggi kadan" Ta yiwa huda bayani a taqaice tana zare idanunta daga sashen da suke. Sauka idonta yayi kan wayarta dake ajiye wadda a qalla ta kusa kwana biyu a wajen. Sam bata da sha'awarta ma don batajin zuwa yanzu tana da wani uzuri da ita. Jib,ayshatu,qannenta da sauran mutanen da takejin sun Ta'allaqa a wuyanta kadai zuciyarta ke mata amsa kuwwar ta nemesu.......tayi sallama da kowannensu.....saidai kuma wani sashen daban yana bata qwarin gwiwar bata da buqatar hakan!. Tana ji a rai zuciya dama jikinta tamkar wani gajeran balaguro ne kawai zatayi daga tata duniyar zuwa wata duniyar,balaguron da bai wuce misalin qifatawar idanu daga rufewar zuwa budewar ba. Bataji kwata kwata cewa wai auren zai zama wani dogon aiki da zata kasa yakiceshi cikin qanqanin lokaci. A yanzun zata zubawa komai da kowa idanu.....kwadin me kwadayi......burin me buri......da tsarin me tsari a kanta ya kwanta.....sannan ne ita kuma zata aiwatar da nata shirin hankali kwance( nikam nace uhmmm....qaddara dai ta rigayi fata🥺😊). Da plate huda ta dawo,wanda tsara zuba abincin gwanin sha'awa. Sabreen tasan duka tayi ne don taci,ta jera soyayyen kifin saman shinkafa da waken,sannan ta mata roban yaji da magi daban. Da kallo kawai tabi plate din,don tasan yafi qarfinta koda duniya ma tana kwance bare yanzu da wani abu waishi abinci baya burgeta. Sallamar kawu rufa'i da sautin muryarsa kadai ya sanya abincin data sanya a bakinta ya tsaya mata cak a maqogaronta,sauran na bakinta kuma taste dinsa ya canza mata,har tana jin ba zata iya taunawashi ba,har sai data tattara dukkan juriyarta sannan ta tauna ta turashi zuwa maqogaronta wanda ta samu ya wuce da qyar,sai kawai ta yanke hukuncin ajiye abincin. Idanunta ya sauka kan kawun sanda take ajiye plate din a qasa,wanda yake jaye da wata mini luxury luggage me azabar kyau da kuma daukan idanu. Koda bakasan me duniya ke ciki ba,koda bakasan darajar abinda yake janye dashi ba tabbas zata fahimci luggage ne me tsada da madaukakiyar daraja. Wajen zama mamma bahijja tayi masa tana sanya nadra ta ajiye masa drink da ruwa. "Ya hidima ya kuma shirye shirye?" Kawun ya furta da muryar dake nuni da zallar farincikin da yake ciki "Alhamdulillah.......ai kune da hidima,tunda mu nan ba abinda zamuyi" Kai kawu rufa'i ya girgiza yana satar kallon sabreen da tunda ta gaidashi bata sake koda kallon sashen da yake ba. "Allah ya yiwa yarinyar nan taurin kai bahijja......idan kinga abubuwan da sukaso gabatarwa zakisha mamaki......har yanzu quruciya ke dawainiya da ita,inda tasan girman matsayi da darajar mutumin da zata aura,na rantse miki saita qare rayuwarta tana godemin.....attajirin matashin da babu irinsa a wannan qarnin da muke ciki?" Dan murmushi kasan momma bahijja tayi,adan zamanta ta fahimci kawun yana sa son abun duniya "Duk bama wannan ba rufa'i,indai har bincikenku ya tabbatar da nagartarsa ai magana ta qare.....dukiya wannan wani abune na daban ai" "Habawa.....idan ana batun nagarta ma da dattako har ayi magana wadannan dattijan?" "To alhamdulillah.....haka akeson ji...." "Yanzu haka ma aike ne......saqo ne na musamman daga surukarta......kaya ne tace a kawo mata da zata sanya a gobe kenan" "Tofa.....ikon Allah,kuma dai?,basa gajiya?"Momma bahijja ta fada duba da irin kudaden da aka narkar,tun daga dukiyar aure har izuwa batun lefen dasu kansu har yanzu basu gama sanin komai da komai dake cikin akwatunan ba. Tana qara ganin girman qaunar da suke gwadawa sabreen din,a gefe guda har ranta tana jin tamkar sabreen din tayi sa'ar inda zata rayu cikin qauna da kulawa. "Wai wai.....ma sha Allah" Momma bahijja ta furta tana daga lafiyayyen applique lace da kudi suka koka qwarai wajen siyensa. Daga qasanshi kuma wata bazin ce data amsa sunanta sai super Sheraton da iya ado da gayu da kashema kai kudi irin na momma bahijja bata taba katarin ganin irinta ba. Daga qarshe set ne na banguls earrings da sarqa da zobensu duka na danyen gold me matuqar daraja(nikam nace masu abu da abinsu). Ko qwaqwqqwaran motsi sabreen batayi ba ballanta ta daga kanta ko zata nuna alamun tasan bidirin da akeyi,har sanda hadiyya tayi sallama tana shigowa falon da guntuwar fara'arta. Sunan kayan kawai ya gaya mata darajar abinda aka sako a ciki saidai hakan bai dadata da qasa harta daga kai ta basu darajar kallo ba,don batajin zata iya rabasu a jikinta. Komai daya fito daga hannunsu duhu yake mata,baya mata haske ko kadan.....musamman da take kyautata zaton kayan sun fito ne daga hannun waccar matar maras daraja. Still shigowar hadiyya bata sakata daga kai ta dubeta. Can qarshen zuciyarta danqare da mamaki,yadda kudi ke iya sauya dabi'un mutanen duniya cikin qanqanin lokaci,duk da wannan karatun ta jima da haddaceshi......kusan shi ya zama sila na sauyawar DUNIYARTA. Hadiyyan ta sauya kamar ba ita ba,abinda bata taba tsammanin zaya faru nan kusa ba. Bata zaqe da yawa ba wanda tasa tasirin karatu ne wala'alla da salon gogewa......hakanan kowanne taku kadan tana yunqurin kutsa kai jikinsu ne. Hadiyya ita ta qarasa daga kayan matsanancin mamaki yana sake kasheta. Hidima sosai suke gwadawa sabreen din kaman rijiyar kudi garesu. Ba wanda yakai me kudi sanin darajar kudi,saidai ga wadannan bataga alamun hakan sam daga garesu ba. "Gashi zakiyi magana da surukarki" Momma bahijja ta fada tana sauke wayarta daga kunne gami da miqawa sabreen. Dan turus tayi tana sauke fararen idanunta akan fuskar momma bahijja din. Muddin wannan matar ce sam bata da sha'awar wata magana da ita. Komai nata bisa gadara ne iko izza da kuma nuna qarfin dukiya,don me zata zauna tana gwada mata tata izzar bayan ba ita ta gayyaceta cikin rayuwarta ba. Idanu sunyi yawa a kanta,don haka ta sanya hannu ta karba tana kauda fuskarta daga kallon idanuwan. Sallamarta kadai ya gaya mata ba wadda take zato bace,cikakkiyar sallamar data saukar da duk wani zafi da zuciya da kuma halshenta suka dauka,saita amsa mata a nutse matuqa "Kina yini lafiya diyata?" Anni ta fada daga nata bangaren jin sabreen din tayi shuru. Karon farko sai taji nauyin matar ya saukar mata,batasan me yasa a iya waya kawai takejin girma da kwarjininta ba......shin itace asalin mahaifiyarsa ko yaya?.....itadin wacece a wajensa?,waccan ma wacece a wajensa?. Iya wannan tambayoyin da bata da amsa kadai suna sakata a jikinta tana jin tabbas akwai wani gagarumin abu birne a qasa.....duk da zuciyarta tana gaya mata ba wani babban abu bane da zai gagari sarrafawarta ba. "Barka da yamma.....lafiya alhamdulillah" Ta hade gaisuwar da amsar tambayarta. "Ma sha Allah" "Naga saqo,na gode" Tayi hanzarin fada,don a cikin ranta takejin bai kyautu ba har sai ta magantu. "Ba komai......inaso ne kawai kiyimin alfarmar sanyasu a duk sanda zaki shigo ahalinmu" Tayi maganar a tausashe cikin kuma nuna kulawa,kulawar data bayyana kanta sosai cikin sautin muryarta "In sha Allah" Ta sake amsa mata "Ina fatan hakan ba takura?" "Ba komai....in sha Allah" "To alhamdulillah......ina roqon ubangiji ya tattara dukkan alkhairanku ga junanku......ya kauda kowacce irin fitina da abunqi a tsakaninku". Batasan me yasa ma......amma har tsakiyar qirjinta taji saukar addu'ar......batayi kuskure ba idan tace kunnuwanta itace mutum ta farko data fara jin addu'ar daga bakinta,sai taji labbanta sunyi nauyi bare su tallafeta ta amsa.....yayin da anni tayi zaton kunya da kawaici suka hanata amsawar......a haka tace ya baiwa momma din wayar. Zuciyarta tayi nisa qwarai da zurfi wajen tunani,har batajin ma meke wakana cikin falon,sai kawai ta yanke nesanta kanta dasu ta hanyar komawa daki kaman yadda ta maida hakan dabi'arta. Bata jima cikin duniyar dakin data maida mazauninta ha nadra ta shigo dauke da wayarta a hannu. "Ana kiranki" Ta fada tana miqa mata wayar. Kamar tace mata ta koma da ita sai ta fasa,ta saka hannu ta karba tana daga kwancen tana duba me kiran. Sunan data gani ya sanyata miqewa ta zauna sosai babu shiri,hannunta na gaggawa wajen amsa kiran ta sakashi a kunnenta "Kicemin kun dawo titi don Allah,kicemin ayshatu ta warke" "Na warke adda......na samu sauqi" Muryar yarinyar ya saukar mata a kunne. Wani hawaye me sanyi ne ya kubce mata,kullum da lamarin yarinyar take kwana take kuma tashi,daga yadda taji muryarta tasan cewa tabbas lafiya cikakkiya ta samu a gareta "Muna cikin sabon gidanmu yanzu aunty.....na gayawa titi bazan yarda na fara ganin kowa ba sai ke". "Yanzu kuwa zaki ganni ayshatu" Ta bata amsa kai tsaye kaman ta manta a wanne yanayi ita din take.....kaman ta manta rabonta da taka qasar waje wasu kwanaki ne masu yawa. Da wani irin excitement ta ajiye wayar,ta zura qafafunta qasan gadon da hanzari zara miqe da nufin shiryawa,sai kuma ta dakata cak saboda dawowa hayyacinta da tayi. Tayi imanin wadannan mutum mutumin har yanzu suna tsaye a qofar gidansu suna gadinta,yawan mutanen dake kai kawo a gidan bai sanyasu sun tafi ba......don ko dazu ita iya jiyo baqin tsagin abbansu suna tambaya a kansu. "Saina fita kota halin qaqa wannan karon......ko meye zai faru saidai ya faru" Ta fadi tana qarasa saukowa,ta kuma fito kai tsaye zuwa ga falon tana nufar doguwar veranda din dake saman wanda tacan zata samu hanyar gangarawa qasa ta koma ainihin dakinsu. _DUNIYA TA na kudi ne_ 08187255862 𝐃 𝐔 𝐍 𝐈 𝐘 𝐀 𝐓 𝐀 𝘡𝘢𝘧𝘢𝘧𝘢𝘣𝘪𝘺𝘢𝘳 ̶B̶O̶O̶K ̶2 ⱧɄ₲Ʉ₥₳ 𝙋𝘼𝙂𝙀 6 Page 06 Batasan gidan ya fara daukan mutane ba sam sai data sauko din. Gomayyar idanuwa sukayi kanta caaa ana qare mata kallo. Kowa da nashi tunanin cikin ranshi,wasu na kallon tsantsra kyan data qara saboda gyaran jiki na musamman data samu tsahon kwanaki daga wajen qaararriyar me gyaran jiki......wasu kuma na mata kallon sha'awa suna fadin inama su ko 'ya'yansu keda wannan sa'ar ta auren irin mijinta?,yayin da wasu nasu kallon na bin qwaqwafi ne hassada da tarin tambayoyin ta yaya KARUWAR GIDA.....WADDA TA GAMA RABA MUTUNCINTA WA MAZAN TITI TA SAMU BABBAN MUTUM.IRIN MUHAMMAD JADDA DIN?. Miskilanci da shariya kusan cikin jininta suke,don haka tayi kaman bata gansu ba ta wuce dakinsu kai tsaye.....ballantana kusan dukansu tana cike dasu. Ba wanda yabi takan rayuwarsu.....qaqa suka kwanta qaqa zasu tashi?,amma sai gasu yanzu zube da sunan sunzo auren yarinyar da basusan yaya ta girma ba?,me taci har takai wadannan shekarun?. A gaggauce ta shirya cikin wata luxury Egyptian abaya datayi masifar karbarta,wadda inda cikin nutsuwarta da hayyacinta take itama ya kamata ace taga yadda rigar ta karbeta. Tun daga nesa kana iya ganin mugun kyan da fatarta tayi,wani irin haske da glowing kawai takeyi,saika rantse da Allah diyar wani hamshaqin ce. Qaramar handbag kawai ta dauka ta jefa wayarta a ciki da dan canjin da zata riqa saboda mota,ta fito daga dakin a nutse tana isowa falon,daidai sannan momma bahijja ta shigo rungume da dinkakkun atamfofin da tasa aka dinkawa su haneefa duk da tarin suturunsu. "Ina zuwa kuma?" Momma din ta jefa mata tambayar tana kallon yadda take komai a gaggauce. Batasan da wanne harshe zata yiwa momma bayanin aysha da muhimmancinta a wajen ta,don haka a taqaice tace "Dubiya zani momma...." "Zuwa ina?.....kuma dubiya a irin wannan lokacin?" Kai ta langabe kadan tana fargabar kada momma din ta hanata fita,don a irin wannan lokacin ita kadai takejin zata hanata fitar ta hanu "Ba niss momma.....ba jimawa zanyi ba". "Nadra ta rakaki,kuma kada ki wuce awa daya" Ta fada tana qarasawa tana zube dinkunan hannun nata saman kujera. Mayafi kawai ta figowa nadra,ta sanya wasu plate shoe nata sannan suka fito. Sam bata damu da yadda idanuwa keci gaba da binta da kallo ba,har wasu na qoqarin gaisawa da ita,a haka ta doshi qofar gidan nasu tana tsara yadda zata kaya tsakaninta da qedarun da aka tsaida a qofar gidan. Tana takawa zuwa qofan tana jin fargabar yau dame zasu zo mata?,don dai yadda takeji a ranta yau koda sama da qasa zasu hade sai ta fita.......don ba wani mahaluqi daya taba saka mata dokar zama cikin gida har haka tsahon rayuwarta......sai yau gashi sama ta ka wani mutum can da baisan ciwonta ko darajarta ba......yanason yayi amfani da giyar kudi ya yiwa rayuwar karan tsaye. Tana tura qofar yana riqeta kana aka qarasa budeta. Fuskar kakkauran mutumin ta bayyana har abun yana bawa sabreen mamaki. Bata taba kawowa a lokacin irin wannan zata sameshi tsaye bakin qofar ba kamar wanda aka tsaiguntawa zata fita......waisu basa zama?,ko basa hutawa da jiddin suna tsaye suna gadin duk wani motsinta. "Good evening madam" Abdulgaffar ya furta cikin matuqar girmamawar nan da suka saba mata magana da ita saidai kuma a dabarance yana matse kowacce hanya da zata iya rabawa ta fice daga gidan. Ta gama karantar motsinsa kaf.......bata wani damu da gaisuwarsa ba ta azawa fuskarta wani irin halakakken bacin rai da kuma d'aurewa "Kiramin boss dinku" Ta bashi umarni nakai tsaye da wani irin sauti da babu wasa ko kadan a ciki. Tanaso ta gwada musu girman abinda zata iya aikatawa.......tanaso ta gwada musu basu ba......koda boss dinsu ma bata daukeshi da wani tarin muhimmanci ba. "Bani da connection dashi......idan zan kirashi saina jira anyimin iso kafin na samu magana dashi......amma ga jordan zai kira miki shi" Abdulgaffar yayi mata bayanin cikin girmamawa yana matsawa da baya. Can qasan ranta mamaki yake kamata,wanne irin girman mulki da izzar kudi gareshi da har yaransa ma ba kowa da kowa keda daman magana kai tsaye dashi ba "Good evening madam.......kiyi haquri ki jira kadan,yanzu in sha Allah zai amsa" Jordan ya fada yana rusuna mata. A ranta tanaso ta gaya musu ne a fili "Qattin banza.....kun zauna kuna yiwa mutum qwaya daya bauta saboda yana da dukiya" Abinda zataso gaya musu kenan ganin yadda jordan ke lalubar muhammad fuad jadda cikin girmamawa. A lokacin yana tsaka da hada duk wasu muhimman abubuwa nashi da kanshi,ba tare da ya bari hidiminsa ya masa ba wato me sunan malam. Akwai wasu abubuwan da da kanshi yake yinsu,duk da tarin hadiman dake gareshi. Yana sanye da fara qal din t.shirt me laushi Vshape neck,hannunta iya dantsensa wanda hakan ya sanya murdaddun damtsensa dake nuna girman daga qarfe da yakeyi suka bayyana,wandon jikinsa ma farinne duka duka tsahonsa iya qaurinsa,sai lausasan fararen flip-flops masu tsananin haske da taushi. Cikin kowanne irin yanayi tsarinsa na dabanne,kai tsaye zaka iya cewa gayu ya ratsa jikinsa da gasken gaske.....koda kuwa bacci zai shiga zaka sameshi neat....komai nashi kuma completed kai kace ba bacci zai kwanta ba. Yadda yake a nutse cikin wani irin tsari haka komai nashi yake kasancewa,waya.yake amsawa wadda ya sakata a hands free ya ajiye saman wani zagayayyen kujera me siffar qwallo dake a gefe. Kadan ya kalli wayar,sai ya fahimci kiran jordan keson shigowa amma yana buqatar izinin haka,don haka ya katse wancan kiran ya bawa kira jordan din dama "Barka da wannan lokaci sir" Jordan yayi maganar cikin girmamawan data bata ran sabreen,ta cika fal da mamakin wanne irin ban girma ne haka kaman yana a gabansa?,ya kasa miqewa da dukka tsahonsa ya amsa wayar. "Yauwa Jordan......ya akayi?" Ya tambayeshi kai tsaye. Sai daya dan daga idanu ya kalli sabreen din da idanunta ke cike tab da fushi,sannan qasa qasa yace "Madam daka tura a yiwa aiki ce keson magana dakai sir" "Madam?" Ya tambaya yanason tuna abun don ba komai yake baiwa muhimmanci ba "Eh sir....." "Bata wayar" Ya umarceshi kai tsaye don ya tuna inda zancan ya dosa. "Ka matsa a wajen idan ka bata" Ya sake fadiwa jordan don bayason yayi involving yaransa cikin abinda bai shafesu ba.....hakanan yana ganin ba girmansa bane su fahimci komai ba. Kaman ba zata karba wayar ba don tana jin kamar ta zuba a qasa data nema magana dashi......saidai kuma girma da martabar inda zataje din ya shafe komai a idanunta,don haka ta sanya nadra ta karbo wayar daga hannunsa sannan ta karba a hannun nadra din,ta taka a nutse tana dan komawa ciki duk da jordan ya matsa daga inda zai iya jinta. A kunnenta ta kara wayar,saidai har kusan shudewar mintuna guda tim ba wanda ya cewa da dan uwansa komai. 𝐃𝐔𝐍𝐈𝐘𝐀 𝐓𝐀 𝘓𝘪𝘵𝘵𝘢𝘧𝘪𝘯 𝘬𝘶𝘥𝘪 𝘯𝘦 08187255862 𝐃 𝐔 𝐍 𝐈 𝐘 𝐀 𝐓 𝐀 𝘡𝘢𝘧𝘢𝘧𝘢𝘣𝘪𝘺𝘢𝘳 ̶B̶O̶O̶K ̶2 ⱧɄ₲Ʉ₥₳ 𝙋𝘼𝙂𝙀 7 Tana tsananin buqatar ta fita,ta kumayi imanin wadannan gumakan ba wanda zai musu magana suji sai wanda ya turosu.....tana jin kuma faduwar fara yin magana dashi. Sanda taji ya motsa da bisa alamun ajiye kiran zaiyi,a nutse ta bude baki ta soma magana dashi da qaramar muryar nan tata me wani irin tone "Ban kasance daya daya daga cikin hajojin kamfaninka ba ballantana ka sanya min masu tsaro na......'yantacciyar d'iya ce kamar kowa,hakanan mutum ce dake da nata tsarin da qa'idojin da ba komai take jurewa ba......ka yiwa wadannan gumakan magana da suyi gaggawar matsawa subar qofar gidanmu". Tsayawa yayi cak da abinda yakeyi,ya harde hannayensa a qirji yana sauraronta da muryar dake nuna tamkar gargadinsa kawai takeyi kai tsaye. Idanunsa ya lumshe kai tsaye na sakanni sannan ya budesu,yana ci gaba da jin qaramin sautinta dake magana cikin yanayi na tsiwa har sai data qarasa maganarta. "Bakisan waye ni ba.....i can't tolerate it,dole ki koyi manners......bawai na zama dani kawai ba,manners akan komai ma,tabbas kina buqatar tarbiyya,Your attitude needs a serious adjustment.....and im not going to put up with anymore nonsense,I won't tolerate any more of your nonsense,its time to get in line" Yayi furucin harshly muryarsa cike da seriousness. Din din din da taji wayar nayi shi ya tabbatar ya yanke kiran. Ta sauke wayar daga kunnenta tana jin wani irin daci yana taso masa tun daga cikin maqogoranta har zuwa saman harshenta. Tabi wayar da kallo ranta yana mugun baci,tana jin maganganun daya gasa mata suna yawo cikin kunnuwanta. Tana jin kamar tayi cilli da wayar ko zata samu sauqin radadin dake cisgar zuciyarta......to amma saita tuna idan tayi hakan bata kyautawa ainihin me wayar ba,wanda shima da alama komai nasa yana yine bisa tsoro da kyakkyawan bin umarni ba tare da sabawa ba. "Kai mishi wayarsa" Tace da nadra tana miqa mata wayar,sannan ta miqe tana gyara jakarta tabi bayan nadra zuwa qofar gidan,tana jin yau saita nuna masa iyakarsa ta hanyar fita,idan yaso ya tashi duniyar a yau kowa ya huta. Nadra ta rigata isa,ta bashi wayar dake ringing,yana duba me kiran yayi hanzarin dagawa tare da matuqar rusunawa yana fadin "Hello sir" Idanunshi suna sauka kan sabreen,sai ya miqe yana sauraron umarni daga wayar yana kuma kallon sabreen wadda ke tafiya cikin tsananin fushi,har kuma ta samu nasarar sanya qafafunta a qofar gidan. "......idan naga sabanin haka ka kuka da kanka" Qarshen maganarsa kenan data jawo hankalinsa zuwa ga sabreen wadda ta dauki hanyar barin layin sosai bata tsaya koda waiwayarsa ba ballantana wayarsa da yakeyi,tana jin bata da lokacinsu gaba dayansu. Da sassarfa abdulgafar ya jefa wayar a aljihunsa ya juya da sassarfa yabi bayanta. Daga yadda yau boss din ya masa magana ya tabbatar akwai magana a qasa. He's speaking seriously,yasan abinda ya fada da gaske yake. "Madam.....ah.....am,madam sorry......listen please" Ya furta bayan ya cimma bayanta. Nuna ma tasan yana biye da ita a wajenta bata lokaci ne,bata da lokacin batawa ta saurareshi daga shi har boss din nasa "Madam please ki tsaya ki saurareni,am going to loose my job.....please listen to me". Maganar ya taba mata zuciya........yanzun nar rashin imaninsa yakai ace ya kori mutum bakin aikinsa saboda wani abu daban ya faru?. Daga yadda yake maganan kawai ya gaya mata da gaske yake fadi,don haka tadan sassauta tafiyar ba tare data kalleshi ba tace "Ina jinka" "Please madam ki koma gida.....kiyi haquri ba yadda muka iya.....haka boss ya tsara......" "Wannan kuma bazai yiwu ba,idan baka da abun fada ka koma yafi maka sauqi" Daga hakan taci gaba da tafiyanta. A nutse take ratsa layin,yayin da idanun 'yan sanya ido ya soma yin caa a kanta. Ba yadda zaka kalleta ita da abdulgaffar din kace ba body guard dinta bane,saboda yake take mata baya yana maida takunsa duk inda ta dauke ba tare da sunsan abinda ya sanya ya biyota ba,take tsegungumi suka fara tashi,masu rade radi akan irin mijin da zata aura a yau suka samu tabbacin hakan Da alama zazzafa ce itama tamkar boss din nasu,ya hanga ya hango babu wani sauran abinda ya rage masa illa ya kira oga farouq,don haka yana biye da itan yayi kiransa,yayi kuma bayani a taqaice. "Turawa hood location ta watsapp...zaizo da mota ya kaita.....idan yazo din give me a call.....zanyi magana da ita" Yayi maganar haushin fu'ad yana kamashi. A ganinsa tunda batu ake na aure koma meye ya kamata ya ajiyeshi a gefe,batun aure ya wuce wasa.....ya kuma wuce tunanin mutum. Wani irin aiki ne da ake yinsa da umarni da kuma doka. Iya tsaiwar da tayi tana jiran ababen hawan da batasan dalilin da yasa duk wanda ta tsaida sai ya wuce ba.....wanda qwarewar aiki irin na abdulgaffar ya sanya yake musu alama me nuna gargadi kan tsaiwar tasu,take suke wucewa abinsu. A hankali motar ta rage gudu tana qarasowa gabansu,wanda tun kafin takai ga qarasowar abdulgaffar ya ganeta. Motocin da dukka suka jibanci familyn muhammad jadda da kuma gidan alhj hamza kibiya ba boyayyu bane,don hatta da plate number dinsu na dabanne da wani irin kebantaccen tsari na daban. Bai bari motar ta qaraso gabansu ba ya kirayi farouq din,sai komai yazo a daidai,isowar motar gabansu da kuma matsawa da yayi daura da ita ya saka wayar a handfree yadda idanunta zasu iya ganin wayar "Ranki ya dade......Allah ya taimakeki,tuba muke,kunyi magana da boss yana cikin fushi ne.......ayi mana alfarma kiyi haquri,ga driver da mota nan ya iso,ki shiga ya kaiki duk inda kikeso,tuba muke,tuba muke" Ya maimaita har sau biyu yana hade tafukan hannayensa guri daya. Batasan me ysaa ba,amma sai taji tasss ta sauka daga fushin da takeji. Yanayin maganarsu dama komai nasu ba daya bane,batasan kuma waye ba......sannan batasan nasabarsa dashi ba.....amma da iya lafuzan bakinsa kadai ta tabbatarwa kanta yasha banban dashi tako ina. Batace komai ba ta soma takawa tana nufar motar da tuntuni suka wagale mata qofar suna tsaye suna jiran isowarta,tadan dubi security din kadan ta kauda kai tana tabe baki. Su kuma a haka rayuwarsu zata qare?,basa da aiki sai ta'ammali da murda murdan garadan da babu rahama akan fuskarsu?,idan kuma suna tsaye sai kace gumaka?,wacce irin rayuwa zata shiga ne?. Da wannan tambayar ta shiga cikin motar suka maida murfin suka rufe. Duk da yadda ranta yake a bade,zuciyar kuma bata tare da komai amma hakan bai hanata fahimtar banbancin inda ta shigo ba. A hankali ta kalli wani sashe na motar,cikin ranta tana jin zallar tsagwaron banbanci. Batayi kuskure ba idan tace tsahon rayuwarta bata taba tsammanin da gaske akwai mota irin wannan a nigeriar mu ba,cikin motar bai mata kama da komai ba saida wani qawataccen madaidaicin falo na alfarma,idan ba yaye labulen window din kayi ba zata ko dan jirin motsin motar kadan ba saika tsammaci cikin wani killataccen falon kake. Taja numfashi a boye tana saukeshi,duk da ita kadaice a nan amma saita killace ganinta. Bangare daya zuciyarta tana bugawa da samun tabbacin lallai da gasken da kawun ke fada su din ba qananun mutane bane......amma ta yaya suke bibiyan rayuwarta?,me yasa sai ita?,me suke tunanin tana dashi wanda zata iya basu?. Amsar dai kamar kowane lokaci.....hasashen kaman na kowanne lokaci shine AKWAI WANI ABU A QASA. Da wani irin makirin narkakken murmushi ta maida murfin qawataccen akwatin ta rufe bayan ta gama ganin suturar alfarmar da aka tsumata da wasu tsatsube tsatsube na musamman da suke a mazaunin matakin farko na fara tunkarar shirin data yiwa rayuwar mutum biyun.......sanadin wato sabreen.....da kuma maqasudin wato muhammad fu'ad. "Komai yayi hajja........suturar million biyu kam baa kashe kudinsu a banza ba.......yanzu zuwaira za'a aika?.....inajin kamar nayi tattaki naje nakai Mata da kaina,don inaso ta fahimci muhimmancin sanya suturar nan" Tayi zancan da wani irin muhimmanci cikin sautinta,tana tuna bayanan bokan da bata dana biyunsa a yanzu haka _".......tana sata a jikinta ta fara zuwa hannu fa hajja......hakanan shi Kansa fu'ad kallon farko da zaiyi mata da suturar zai jarabtu da sonta,abinda zai bada damar gudanar da aikinmu cikin sauqi,zai karbi komai daga hannunta yaci ya kuma sha ba tare da wani matsala ko tangarda ba"_ Murmushi hajja ta saki tana dora qafarta daya saman daya "Tafiyar zuwaira ita daya yana nuna aiken bame daraja bane,hakanan zuwanki da kanki zai jefa shakku a idanun mutanen da hankulansu ke kanmu irin aminatu hamza kibiya......wannan saqon babbar aminiya kuma amintacciya ya kamata ta isar dashi" Murmushi me sauti ya qwacewa maamah,ta bawa hajja hannu suka tafa tana fadin "Allah yabar mutum da nasa.......bari na yiwa usama magana" Ta fadi tana dauko wayarta dake ajiye gefe ta fara lalubar number wayar usaman. Zuwanta wajen aysha da dawowarta....farincikin data samu na ganin yarinyar ta dawo cikin cikakken hayyacinta da wata lafiya data sanya kumatunta cikowa shine ya haifar da sakewar fuskarta,ya kuma saka mata farincikin da ta kusa mantawa da abinda ke tunkararta a gobe. Kallon masu kallo da idanun masu sanya idanu tun daga qofar gidansu da lafiyayyar motar ta ajiyeta bai dadata da qasa ba,har zuwa sanda ta isa tsakar gidan,ta kama matakala tana haurawa zuwa saman nasu. Tana sanya qafarta sukayi kacibus da momma dauke da tray da lemuka da ruwa akai. "Yauwa yanzu nake shirin kiranki......kina da baqi suna qasa,ki hanzarta ki samesu" Ta gaya mata tana rabata zata wuce "Baqu momma?,su waye?,daga ina kuma?" "Kinga duka wadannan tambayoyin ki adanasu idan kinje kyayi musu.....me lalle ma ke take jira tunda kika fita". Ambaton sunan me lalle saiya fara dagula mata lisssafi,bayan dirje fatar da aka dameta dashi na kwanaki kusan goma yanzu kuma wani me lalle ne na daban zata zauna yi?,salon a bata mata hannu da qafar da bata shirya diga musu komai ba?. Ganin momma tayi gaba har tana gangarawa qasan stairs din ya sakata itama ta laqume dukka tambayoyinta tana wucewa ciki. Zuciyarta fal da saqe saqe ta sauya abayar jikinta zuwa wata sassauqar doguwar Riga cotton me gajeran hannu data zauna daidai jikinta,ta dauki qaramin hijab daya tsaya mata iya kafadu ta maqala ta juyo tana saukowa. Dukkansu su biyun suka amsa mata sallamar idanunsu a kanta "Tubarkalla ma sha Allah" Zuwaira da tayo rakiya ta qarfi da yaji don ba haka Hajja taso ba ta furta kyan sabreen yana bugar da ita. Duk yadda take jin hira da yadda aka tsara komai bata taba kawowa kyan yarinyar yakai haka ba,ta dauka maamah din nada tsananin wayo......zata dauko yarinyar da bata da cikakken siffa gudun juyewar reshe da mujiya. A iya sanin data yiwa halittar 'ya'ya maza masu jarabtuwa da kyakkyawar mace komai kamewarsu kuwa. Sanda suka iso gidan batayi tunanin gidan masu matsakaicin qarfi da gata irin wannan yana qunshe da kyakkyawar sura har haka ba,taci gaba da qare mata kallo yadda shape me qirar Coca-Cola ya fita sosai ta cikin rigar ta wajen qugunta. Duk kallon da zuwaira ke qare mata hankalinta baikai ba,saboda hankalinta daya tafi akan hajja da suka fara hada idanu. Ta yaya zata manta fuskar matar?,bayan tana a wajen sanda sukazo da tallar qazamtacciyar hajarsu?,kuma kusan itace tafinta a wajen matar dake iqirarin mahaifiya take a wajensa. Yadda sabreen din ta tsareta da idanu tana zama a dosane a hannun kujera irin yadda takeyi idan zuwan mutum magana ko mu'amala dashi baiyi mata ba "Sannu ko?" Hajja ta fada tana qaqaro murmushin dole. Wani irin kishi me girma ya sauko mata akan Sabreen din. A haduwarsu da suka taba yi qwaya biyu hankalinta bai taba kaiwa kan sassanyan kyan da yarinyar ke dashi ba. Wani irin halakakken kyau dake boye a kowanne sashe da kuma halittarta. Anya wannan ba kuskure bane?,idan har tayi saken daya fadawa sonta rabasu kuwa zai zama abu me sauqi kuwa?. Tabbas bata taba kula da wannan kyan ba,wanda inda tasan dashi tana da dukkan makaman da zata rusa tafiyar........a yanzu bayan komai yayi nisa ta yaya zata katse wannan wasan da bata taba ganin abinda maamah ta ciwa buri a kansa har haka ba. "Yauwa sannu" Sabreen ta maida mata da salon yadda tace da ita. Haka kawai taji ba zata iya gaida matar ba,tun a waccar ranar duk wata kima martaba da kuma mutunci da ake ganin dan adam me girma da shekaru nasu duka su biyun suka kwaranye mata. "Ya gida ya shirye shirye?" Hajjan ta sake dauriyar fada yadda sabreen din ke shan qamshi yana qara qona mata rai,amma duka wannan ba komai bane......tasan s nan kusa zata fahimci wace ita?kuma su waye su. "Alhamdulillah" Ta sake amsa musu. Kai tsaye hajja ta gabatar da abinda ya kawosun,da dukkan alamu sun nuna ba'a maraba dasu ata nan din "Saqone daga mamarki" Hajja ta fadi tana turawa zuwaira akwatin,ita kuma tana sadar dashi xuwa ga sabreen dake binsu da idanu. 𝐃𝐔𝐍𝐈𝐘𝐀𝐓𝐀 𝘭𝘪𝘵𝘵𝘢𝘧𝘪𝘯 𝘬𝘶𝘥𝘪 𝘯𝘦 08187255862 𝐃 𝐔 𝐍 𝐈 𝐘 𝐀 𝐓 𝐀 𝘡𝘢𝘧𝘢𝘧𝘢𝘣𝘪𝘺𝘢𝘳 ̶B̶O̶O̶K ̶2 ⱧɄ₲Ʉ₥₳ 𝙋𝘼𝙂𝙀 10 Page 10 Can cikin tsakiyar kanta maganganun mutane ke mata yawo sanda motar ke tafiya cikin nutsuwa saman lafiyayyar kwaltar dake shimfide a kanta. Muryoyin mutane daban daban da sukayi mata fadan shiga gidan miji wai a cewarsu "Allah yasa dai ki iya zama......don zaman aure daban da zaman bariki,zaman gidan miji daban da yawon bariki" Muryar bibo kenan da nata salon fadan da yafi kama da turun mutuwa "Da dadi ba dadi kiyi haquri ki zauna......Allah yasa mutuwa ce zata raba,kiji kiqi ji,ki gani kiqi gani" Muryar daada kenan wadda ta kama hannuwanta tana fada muryarta a sanyaye. Ko da can ba zatace ga wani mummunan abu da daada ta taba musu ba,ita dai barta da shariya da rashin shiga lamari da sabgar kowa cikin gidan. Idan ka ganta kuwa a ciki to tabbas abu yaci tura,amma bibo da yaabi koda dan wani akeyi suna iya ara su yafa tun usul. "Mommaa......nadra.....haneefa.....huda" Sunayen data iya kirawa momma kenan sanda take yunqurin sakata a cikin motar da zata yi musu jagora zuwa inda zasuje. "Ina sane dasu......kuna su din ba nauyinki bane" Ta amsa masa a tausashe. Ta cikin lafayar jikinta take iya hangen yadda motar ke tsala gudu abinta,amma saboda lafiyar motar da irin tsarin da akayi mata zaka rantse ba gudun takeyi ba. Ta maida idanunta ta lumshe,wasu hawaye da batasan sanda suka taru ba suka biyo kuncinta suka diga bayan hannunta dake ajiye saman cinyarta. Har yanzu dai ta kasa gasgata abinda take gani,har yanzu ta kasa gasgata abinda kunnuwanta da zuciyarta ke nanata mata. Da gaske mutumin nan yaci galaba a kanta da dukka tsarikansa.....da gaske shike da nasara ba ita ba.......da gaske ya cinye wasan a wannan gabar.....saidai kuma hakan baya nufin zaita nasara kenan a kanta,hakan baya nufin ta fadi kenan har abada.....lallai zata canza labarin......zata canza qaddarar da dukkan iyawarta. "Gidan mamarshi zamu fara shiga.......sai gidan riqonsa,kamar haka matar data shigo dazu tace ko?" Daada ta fadi tana dan duban momma bahijja da hannun sabreen yake cikin nata. "Eh haka ne" Ta amsa mata idanunta sauke kan faffadan sabon gate din gidan maamah dake nuna zallar dukiyar dake narke cikin gidan. A nutse jerin gwanon motocin suka cusa kai makekiyar harabar gidan data kasance mafarkin maamah na shekara da shekaru,gidan daya dauki hankula da bakunan dukkan jama'arta dake hulda da ita. Gidan da a cikin ranta ita kanta ta gamsu da dukiyar daya lashe,amma zuciyarta bata gama nutsuwa da hakan ba saboda har yanzu gidan alhj hamza kibiya da iyalinsa yafi nata girma yalwa da kuma tsari,ba tare data duba yawan da suka darata dashi ba,da kuma yawan al'umman da gidan ke dauka suke riqo a yanzu haka. Tunda motar ta tsaya a parking lot na gidan gabanta yake wani irin faduwa,ta maida idonta ta lumshe tana sauraren bugun da zuciyarta keyi da bata taba jin irinsa ba,sai taji bugun har kusa da maqogoronta. Sake runtse idanunta tayi sanda momma bahijja ke fadin ta fito,tana jin bugun zuciyar na sake daduwa amma kuma ta rasa me ya kamata ta karanta?,wacce addu'a ce ta dace da irin wannan yanayin da takejin kanta a ciki?. Riqon hannunta da momma din tayi shine ya sassauta mata abinda takeji kadan,ta sake riqe momma din itama da kyau ba tare tasan ta yadda zata gaya mata abinda takeji cikin qirjinta ba. A dan hanzarce ta shigo dakin nata,sannan ta maida qofar ta kulle ta kuma murza key. Da dan hanzarin still ta isa gaban madubin nata dake manne da wasu lafiyayyun lockers. Ta murza daya daga ciki ta bude ta,sannan ta saka hannu ta ciro baqar ledar dake a ciki ta dora saman madubi. Ko ina a jikinta amsawa yakeyi da wani irin doki da son fara aiwatar da nata aikin,a yau batasan sau dubu nawa tana addu'ar samun wannan sa'ar ba......batasan sau nawa ta roqi samun nasara a wannan ranar ba,nasarar da indai ta rasata kamar wadancan kwanakin ta tabbatar komai zaizo mata da wahalar gaske.....batasan kuma ta yadda zata tari abun ba. Kusan leda shidda ce,kowacce sai data kunceta sannan ta saka hannu ta fara ciro kayan ciki. Kusan tarkace ne a idanun me kallo,amma a wajen maamah gwara rashin million dubu da rasa daya daga cikin kayan. Wasu kwalabe ne masu dauke da wani irin baqin abu a ciki,wani kuma kore kore ne,saidai yana da dan qamshi qamshi kadan a ciki mara qarfi. Ta bude kowanne ta tsiyaya cikin tafin hannunta,ta kuma mulke hannun nata da kyau kamar yadda aka umarceta da tayi,sannan ta maida komai muhallinsa kamar bata taba komai ba cikin dakin. Gaban madubin ta tsaya tana qoqarin controlling kanta da daidaita nutsuwarta. Idanun ta fes cikin fuskarta tana maganar zucci da kanta da kanta,wanda batayi wani nisa ba knocking din da ake mata ya isa kunnuwanta. Adan fusace tace tambaya don bata buqatar doguwar mu'amala da kowa har sai wadda tayi shirin saboda ita ta iso "Zuwaira ce" Ta bata amsa a tsanake. "Sun iso,suna falon qasa sun......." "Gani nan" Ta tari numfashin zuwairan ba tare data jira sauran bayaninta ba. Ba sauran bayaninta take da buqatar ji ba,tunda taji abinda take buqatar jin,ta waiwaya tana zura takalmanta data cire tare da kallon tsadajjen mayafin data lullube jikinta dashi ta tabbatar ya zauna a jikinta......ya sanyata tayi kwarjini da wata irin kamala da sam zai wahala ka kawo wani abu me muni a kanta. Kyanta ya bayyana.....kamanninta da musaddiq sosai,yanayin jin dadin da kulawar data samu wadda take rainawa ta sake sanyawa jikinta ya murje sosai,hutu da quruciya sun bayyanar mata. Murmushi ta sakarwa kanta da kanta,sannan ta juya a hankali tana fita a dakin. Tun daga saman stairs din take raba idanunta tana son hangota. Bata wani sha wahala ba,ta hangeta zaune saman lallausan carpet din da aka qawata tsakiyar falon dashi. Qafafunta a tanqwashe suke,kanta a qasa cikin shigar laffayar da tazo mahadin lace din da aka zauna akyi dukka adon jikinsa da hannu(handmade lace),kamar yadda lafayar jikinta itama duk wani zare da duwatsun jiki da hannu aka gameshi. Abune na masu dashi,ba wani cikar jama'a masu yawa ko cinkoso,kowa yana zaune a nutse,yayin da gaisuwa ke wakana tsakaninsu momma da jama'ar da suka samu cikin falon. Da wani irin kirki na gasken gaske saman fuskarta,faffadan murmushi da fara'a me nuna tsantsar maraba da baqo ta iso rukunin kujerun tana furta "Lale maraba......sannunku da zuwa......sannunku da qoqari" Da murmushi a fuskar momma ta amshe maraban tana duban maamah tsaf tare da karantar yanayinta. "Bari na zauna kusa da diyata" Ta fadi tana zama kujerar dake kusa da sabreen din. Gaisuwa akayi cikin mutunci dason nuna ainihin zallar kirkinta,suka gabatar mata da amanar sabreen tare da dan qaramin jawabin girmama kowa ga sabreen din "Itama diyata ce ai tunda yarona take aure,kuma in sha Allah zakuyi alfahari da hada alaqa damu,Allah ya bada zaman lafiya,shi kuma Allah ya tayashi riqo" Maamah ta furta cikin zaquwa da gajiya da bayanan. So take kawai ta isa ga muradinta. "Am nace ba.....idan ba damuwa inason ganin diyata a kebance,minti biyar don Allah" Maamah ta fada tana murmushi. Ba tare da tunanin komai ba ko kawo komai ba momma bahijja tace "Bismillah mana......haba hajiya ai diyarku ce" Daada ta fadi yadda momma din ta karbi sabreen yana burgeta. Duk da tayi gaba zuwaira ke mata jagora zuwa wani daki na daban a saman benen.....amma saita dinga jin wani irin yanayi yana bibiyar gabobinta. Kasa zama tayi,tana a tsaye sanda taji zuwaira taja musu qofar ta fice. "Zauna mana.....ki yaye wannan lullubin kan naki......don fahimtata nakeso kiyi sosai tamkar yau ne karon farko da kika fara fahimta ko haddace wani abu a rayuwarki" Tayi maganar cikin jerarrun kalmomin da kana jinsu zakasan ko meye zata fada yana da matuqar muhimmanci a wajenta. Sai data fara janye lullubin nata baya,sannan ta sulale a wajen ta zauna. Tana jin kamar babu wani sauran qwarin gwiwa daya rage mata a rayuwa,duk da yadda take kokawa da zuciyarta da qoqarin qarfafawa kanta gwiwa. "To alhamdulillah.......komai ya kammala,kuma komai yazomin da sauqi fiye da yadda nayi zato ko kuma tsammani........ina fata baki manta meye manufar aurenmu ba?" A nutse sabreen din ta daga kai sannan ta zube mata idanunta saman fuskarta. Kallonta tayi na second kusan goma sannan ta gyada kai "Da kyau.....da farko abinda zan fara gaya miki shine abinda na maimaita miki a baya.......qaidar contract dina na farko shine sirri.......inason sirri,don muddin aikin nan ya fita daga da'irar sirri zuwa wata da'ira ta daban.....to tamkar kin wargaza rayuwarki da hannunki ne......bayan taki rayuwar da kika wargaza kuma......kin wargaza ta 'yan uwanki suma...." Daga ma maamah hannu tayi da hanzari tana zare idanunta daga kanta "Ki tsaya iya kan ameenatu kawai......huda,nadra da haneefa,tabasu ko sako sunansu cikin sabgarki da ameenatu tamkar ganganci ce" "Da kyau!" Maamah ta furta tana sakin murmushi,abubuwa biyu zuwa uku suna jan hankalinta. Gyara zamanta tayi tana ci gaba da murmushi "Ashe ameenatu ce....abu yayi kyau..ameenatu ta bata,wata ameenatun zata gyara,wannan abun yayimin dadi.......qwarin gwiwarki da rashin sarewarki ya burgeni......kariyar da kike bawa qannenki tana da yawa,kuma ita dai ta isa ta bani yaqini da tabbacin ba zaki bari a samu failure ba ko don saboda su......." "Shiga maganarki kai tsaye" Sabreen ta fadi mata tana kauda kanta zuwa wani sashe na daban. Idanu maamah tadan zuba mata har yanzu tana murmushi,sai kuma ta miqa hannu ta zaro wata paper da abun rubutu ta ajiye a gabanta. "Inaso ki rubuta adadin kudaden da kike da burin mallaka a rayuwarki......ni kuma zan mallaka miki su a madadin sadakin aikinki,zan kuma qara miki kwatankwacinsu muddin komai yayi daidai". Fararen manyan idanunta ta daga ta watsawa maamah su,karon farko da idanun suka yiwa maamah din wani kwarjini da bata taba jin irinsa ba. Murmushin da ya subuce kuma a fuskar sabreen ya sanya mata kokwanto "Ki fadi magana me muhimmanci saboda mutanen dake zaman jiranki a qasa" . Maganar tata tadan daure mata kai,a nata ganin ba wata magana da zata zama me muhimmanci a wajen sabreen sama da maganar kudin aikinta,wanda take ganin shi kadai ya isa ya bata azama akan aiwatar mata da komai. To amma akance......shi yaqi dan zamba ne,don haka ta gyada kai 𝗗𝘂𝗻𝗶𝘆𝗮𝘁𝗮 𝗻𝗮 𝗸𝘂𝗱𝗶 𝗻𝗲 𝟬𝟴𝟭𝟴𝟳𝟮𝟱𝟱𝟴𝟲𝟮 𝐃 𝐔 𝐍 𝐈 𝐘 𝐀 𝐓 𝐀 ̶𝗕̶𝗢̶𝗢̶𝗞 ̶𝟮 ⱧɄ₲Ʉ₥₳ 𝙋𝘼𝙂𝙀 𝟭𝟭 𝗣𝗮𝗴𝗲 𝟭𝟭 "𝗡𝗮𝗷𝗶 𝗱𝗮𝗱𝗶 𝗱𝗮 𝗸𝗶𝗸𝗮 𝘇𝗮𝗺𝗮 𝗺𝗲 𝗹𝘂𝗿𝗮 𝗮𝗸𝗮𝗻 𝗸𝗼𝗺𝗮𝗶,𝘄𝗮𝗻𝗻𝗮𝗻 𝘇𝗮𝗶 𝘀𝗮𝗻𝘆𝗮 𝗸𝗼𝗺𝗮𝗶 𝘆𝗮𝘇𝗼 𝗱𝗮 𝘀𝗮𝘂𝗾𝗶........𝗮𝗶𝗸𝗶𝗻𝗮 𝗺𝗲 𝘀𝗮𝘂𝗾𝗶 𝗻𝗲 𝗶𝗱𝗮𝗻 𝗸𝗶𝗻𝗯𝗶 𝘆𝗮𝗱𝗱𝗮 𝗻𝗮𝗰𝗲 𝗺𝗶𝗸𝗶,𝗰𝗶𝗸𝗶𝗻 𝘄𝗮𝘁𝗮𝗻𝗻𝗶 𝗸𝗮𝗱𝗮𝗻 𝗺𝗮 𝗸𝗶𝗻𝗮 𝗶𝘆𝗮 𝗸𝗮𝗺𝗺𝗮𝗹𝗮𝘄𝗮 𝗸𝗶 𝘄𝘂𝗰𝗲 𝗮𝗯𝗶𝗻𝗸𝗶,𝗮𝗸𝘄𝗮𝗶 𝗻𝗮 𝘀𝗮𝘄𝗮 𝗮 𝗮𝗯𝗶𝗻𝗰𝗶,𝘀𝗮𝗶𝗻𝗮 𝗿𝘂𝘄𝗮𝗻 𝘄𝗮𝗻𝗸𝗮,𝘀𝘂 𝗸𝗲𝗻𝗮𝗻 𝗱𝗮 𝗻𝗮𝗸𝗲 𝗱𝗮 𝗯𝘂𝗾𝗮𝘁𝗮𝗿 𝗮 𝗸𝗼𝘄𝗮𝗰𝗰𝗲 𝗿𝗮𝗻𝗮 𝗸𝗼𝗱𝗮 𝘀𝗮𝘂 𝗱𝗮𝘆𝗮 𝗻𝗮𝗰𝗶𝗻 𝘆𝗮 𝘀𝗵𝗶𝗴𝗮 𝗰𝗶𝗸𝗶𝗻𝘀𝗮,𝗻𝗮 𝘄𝗮𝗻𝗸𝗮𝗻 𝗸𝘂𝗺𝗮 𝘆𝗮 𝗸𝗮𝘀𝗮𝗻𝗰𝗲 𝗮 𝗰𝗶𝗸𝗶𝗻 𝗿𝘂𝘄𝗮𝗻 𝘄𝗮𝗻𝗸𝗮𝗻𝘀𝗮,𝗶𝗱𝗮𝗻 𝗻𝗮 𝘀𝗮𝗺𝘂 𝘄𝗮𝗻𝗻𝗮𝗻 𝘀𝗮𝘂 𝗱𝗮𝘆𝗮 𝘁𝗮𝗸 𝗮 𝗿𝗮𝗻𝗮 𝗺𝗮 𝘆𝗮 𝘄𝗮𝗱𝗮𝘁𝗮𝗿. 𝗜𝗻𝗱𝗮𝗶 𝗵𝗮𝗸𝗮𝗻 𝘆𝗮 𝘀𝗮𝗺𝘂 𝗶𝗻𝗮 𝗺𝗲 𝗺𝗶𝗸𝗶 𝗮𝗹𝗯𝗶𝘀𝗵𝗶𝗿 𝗱𝗶𝗻 𝗸𝘄𝗮𝗻𝗮 𝗰𝗮𝘀𝗮'𝗶𝗻 𝘄𝗮𝘁𝗮𝗻𝗻𝗶 𝘂𝗸𝘂 𝗸𝗮𝗰𝗮𝗹 𝗸𝗼𝗺𝗮𝗶 𝘇𝗮𝗶 𝘀𝗮𝘂𝘆𝗮 𝗱𝗮𝗶𝗱𝗮𝗶 𝗱𝗮 𝘆𝗮𝗱𝗱𝗮 𝗻𝗮𝗸𝗲𝘀𝗼......𝗱𝗮𝗴𝗮 𝗿𝗮𝗻𝗮𝗿 𝗸𝗶𝗻 𝘇𝗮𝗺𝗮 '𝘆𝗮𝗻𝘁𝗮𝗰𝗰𝗶𝘆𝗮.....𝗮𝗸𝘄𝗮𝗶 𝗸𝗮𝘆𝗮𝗻 𝗮𝗶𝗸𝗶𝗻,𝗴𝗼𝗯𝗲 𝗯𝗮𝘀𝗮𝗶 𝗷𝗶𝗯𝗶 𝗯𝗮 𝘇𝗮𝗻 𝗮𝗶𝗸𝗼 𝗮𝗺𝗶𝗻𝘁𝗮𝗰𝗰𝗶𝘆𝗮𝘁𝗮,𝗸𝘂𝗺𝗮 𝘇𝗮𝘁𝗮 𝘁𝗮𝘆𝗮𝗸𝗶 𝘇𝗮𝗺𝗮 𝗻𝗮 𝘄𝗮𝗱𝗮𝗻𝗻𝗮𝗻 𝗸𝘄𝗮𝗻𝗮𝗸𝗶𝗻 𝗮 𝗺𝗮𝘇𝗮𝘂𝗻𝗶𝗻 '𝘆𝗮𝗿 𝗮𝗶𝗸𝗶 𝗵𝗮𝗿 𝗸𝗶 𝗸𝗮𝗺𝗺𝗮𝗹𝗮 𝗮𝗶𝗸𝗶𝗻𝗸𝗶 𝗸𝗶𝘆𝗶 𝗴𝗮𝗯𝗮........𝘆𝗮𝗱𝗱𝗮 𝘇𝗮𝗸𝗶 𝘇𝗮𝘂𝗻𝗮 𝗱𝗮 𝗳𝘂𝗮𝗱 𝗸𝘂𝗺𝗮 𝘄𝗮𝗻𝗻𝗮𝗻 𝘇𝗮𝗯𝗶𝗻𝗸𝗶 𝗻𝗲.......𝘀𝗮𝗶𝗱𝗮𝗶 𝗸𝘂𝗺𝗮 𝘇𝗮𝗻 𝗴𝘂𝘁𝘀𝘂𝗿𝗮 𝗺𝗶𝗸𝗶 𝗸𝗮𝗱𝗮𝗻 𝗱𝗮𝗴𝗮 𝗵𝗮𝗹𝗮𝘆𝗲𝗻𝘀𝗮 𝗱𝗼𝗻 𝗸𝗶 𝗸𝗶𝘆𝗮𝘆𝗲 𝗸𝘂𝗺𝗮 𝗸𝗼𝗺𝗮𝗶 𝘆𝗮𝘇𝗼 𝗺𝗶𝗸𝗶 𝗱𝗮 𝘀𝗮𝘂𝗾𝗶......" "𝗕𝗮𝗯𝘂 𝗯𝘂𝗾𝗮𝘁𝗮" 𝗧𝗮 𝗳𝗮𝗱𝗮 𝗸𝗮𝗻𝘁𝗮 𝘁𝘀𝗮𝘆𝗲,𝘀𝗮𝗻𝗻𝗮𝗻 𝘁𝗮 𝗺𝗶𝗾𝗲 𝘁𝘀𝗮𝘆𝗲 𝘁𝗮𝗻𝗮 𝗴𝘆𝗮𝗿𝗮 𝗹𝘂𝗹𝗹𝘂𝗯𝗶𝗻𝘁𝗮. 𝗪𝗮𝗻𝗶 𝗶𝗿𝗶𝗻 𝗺𝗮𝗺𝗮𝗸𝗶 𝗸𝗲 𝗵𝗮𝗷𝗶𝗷𝗶𝘆𝗮 𝗱𝗮 𝘇𝘂𝗰𝗶𝘆𝗮𝗿𝘁𝗮 𝘀𝗮𝗻𝗱𝗮 𝘁𝗮𝗸𝗲 𝘀𝗮𝘂𝗸𝗼𝘄𝗮 𝗱𝗮𝗴𝗮 𝘀𝗮𝗺𝗮𝗻,𝗯𝗮𝗻𝗱𝗮 𝘁𝗮𝗻𝗮 𝗸𝗮𝗺𝗮 𝗾𝗮𝗿𝗳𝗲𝗻 𝘀𝘁𝗮𝗶𝗿𝘀 𝗱𝗶𝗻 𝘄𝗮𝗹𝗮 𝗮𝗹𝗹𝗮 𝘇𝗮𝘁𝗮 𝗶𝘆𝗮 𝗵𝗮𝗿𝗱𝗲𝘄𝗮. 𝗔𝗻𝘆𝗮 𝗸𝘂𝘄𝗮 𝘄𝗮𝗻𝗻𝗮𝗻 𝗱𝗶𝗻 𝗨𝗪𝗔 𝗖𝗘?,𝗨𝗪𝗔 𝗖𝗘 𝗰𝗶𝗸𝗶𝗻 𝗵𝗮𝗹𝗶𝘁𝘁𝗮𝗿 𝗯𝗶𝗹'𝗮𝗱𝗮𝗺𝗮?,𝗸𝗼 𝗸𝘂𝘀𝗮 𝘂𝘄𝗮 𝗰𝗲 𝗰𝗶𝗸𝗶𝗻 𝘄𝗮𝗻𝗶 𝗷𝗶𝗻𝘀𝗶 𝗸𝗼 𝗵𝗮𝗹𝗶𝘁𝘁𝗮 𝘁𝗮 𝗱𝗮𝗯𝗮𝗻?. 𝗕𝗮𝘁𝗮𝘀𝗮𝗻 𝘁𝗮𝗻𝗮 𝗯𝗶𝘆𝗲 𝗱𝗮 𝗶𝘁𝗮 𝗯𝗮 𝘀𝗮𝗶 𝗱𝗮𝘁𝗮𝗷𝗶 𝗺𝘂𝗿𝘆𝗮𝗿𝘁𝗮 𝘀𝗮𝗻𝗱𝗮 𝘁𝗮𝗸𝗲 𝘁𝘀𝘂𝗴𝘂𝗻𝗻𝗮𝘄𝗮 𝗴𝗮𝗯𝗮𝗻 𝗺𝗼𝗺𝗺𝗮 𝗯𝗮𝗵𝗶𝗷𝗷𝗮 𝗱𝗼𝗻 𝘁𝗮𝘀𝗮𝗻 𝘁𝗮 𝗾𝗮𝗿𝗮𝘀𝗼. 𝗕𝗮 𝘇𝗮𝘁𝗼 𝘁𝗮 𝘁𝘀𝗶𝗻𝗰𝗲𝘁𝗮 𝗮 𝗴𝗮𝗯𝗮𝗻𝘁𝗮 𝘁𝗮𝗻𝗮 𝗳𝗮𝗱𝗶𝗻 "𝗟𝗮𝗹𝗹𝗮𝗶 𝘆𝗮𝗿𝗼𝗻𝗮 𝘆𝗮 𝗱𝗮𝗰𝗲,𝗻𝗮𝘆𝗶 𝗳𝗮𝗿𝗶𝗻𝗰𝗶𝗸𝗶 𝗱𝗮 𝘀𝗮𝗺𝘂𝗻 𝘀𝘂𝗿𝘂𝗸𝗮 𝗶𝗿𝗶𝗻 𝘄𝗮𝗻𝗻𝗮𝗻....𝗔𝗹𝗹𝗮𝗵 𝘆𝗮𝘆𝗶 𝗺𝗶𝗸𝗶 𝗮𝗹𝗯𝗮𝗿𝗸𝗮" 𝗧𝗮 𝗾𝗮𝗿𝗮𝘀𝗮 𝗳𝗮𝗱𝗮 𝘁𝗮𝗻𝗮 𝗮𝘇𝗮 𝗵𝗮𝗻𝗻𝘂𝗻𝘁𝗮 𝘀𝗮𝗺𝗮𝗻 𝗸𝗮𝗻 𝘀𝗮𝗯𝗿𝗲𝗲𝗻 𝗱𝗮 𝘀𝗶𝗴𝗮𝗿 𝘀𝗮𝗻𝘆𝗮 𝗮𝗹𝗯𝗮𝗿𝗸𝗮. 𝗬𝗮𝗺𝗺𝗺𝗺 𝘁𝗮𝗷𝗶 𝘄𝗮𝗻𝗶 𝗶𝗿𝗶𝗻 𝗮𝗯𝘂 𝘆𝗮𝗻𝗮 𝗯𝗶𝗻 𝗸𝗼𝘄𝗮𝗻𝗻𝗲 𝘀𝗮𝘀𝗵𝗲 𝗻𝗮 𝗷𝗶𝗸𝗶𝗻𝘁𝗮. 𝗖𝗶𝗸𝗶𝗻 𝗸𝗼𝘄𝗮𝗻𝗻𝗲 𝗵𝗮𝗿𝗯𝗮𝘄𝗮 𝗷𝗶𝗻𝗶 𝗱𝗮𝗸𝗲 𝘇𝗮𝗴𝗮𝘆𝗮𝘄𝗮 𝗴𝗮 𝗷𝗶𝗷𝗶𝘆𝗼𝘆𝗶𝗻𝘁𝗮 𝘄𝗮𝗻𝗶 𝗶𝗿𝗶𝗻 𝘀𝗮𝗾𝗼 𝗱𝗮 𝘀𝗮𝘂𝘆𝗲 𝘀𝗮𝘂𝘆𝗲 𝘀𝘂𝗸𝗮 𝗳𝗮𝗿𝗮 𝗮𝗳𝗸𝘂𝘄𝗮 𝗱𝗮 𝘄𝗮𝗻𝗶 𝗶𝗿𝗶𝗻 𝘀𝗮𝘂𝗿𝗶 𝗱𝗮 𝗸𝘂𝗺𝗮 𝗴𝗮𝗴𝗴𝗮𝘄𝗮 𝗺𝗲 𝘆𝗮𝘄𝗮𝗻 𝗴𝗮𝘀𝗸𝗲 "𝗔𝗹𝗹𝗮𝗵 𝘆𝗮𝘆𝗶 𝗺𝗶𝗸𝗶 𝗮𝗹𝗯𝗮𝗿𝗸𝗮" 𝗧𝗮 𝘀𝗮𝗸𝗲 𝗺𝗮𝗶𝗺𝗮𝗶𝘁𝗮 𝗸𝗮𝗹𝗺𝗮𝗿 𝘀𝗮𝘂 𝘂𝗸𝘂 𝗱𝗼𝗻 𝘁𝗮𝗻𝗮𝘀𝗼𝗻 𝗮𝗱𝗮𝗱𝗶𝗻 𝘀𝗮𝗸𝗮𝗻𝗻𝗶𝗻 𝘀𝘂 𝗰𝗶𝗸𝗮 𝗸𝗮𝗳𝗶𝗻 𝘁𝗮 𝗱𝗮𝘂𝗸𝗲 𝗵𝗮𝗻𝗻𝘂𝗻 𝗻𝗮𝘁𝗮 𝗱𝗮𝗴𝗮 𝘀𝗮𝗺𝗮𝗻 𝗸𝗮𝗻𝘁𝗮 "𝗔𝗺𝗲𝗲𝗻 𝘆𝗮 𝗔𝗹𝗹𝗮𝗵......𝗮𝗺𝗲𝗲𝗻 𝘆𝗮 𝗿𝗮𝗯𝗯𝗮𝗹 𝗔𝗮𝗹𝗮𝗺𝗶𝗻" 𝗠𝘂𝘁𝗮𝗻𝗲𝗻 𝘄𝗮𝗷𝗲𝗻 𝗸𝗲 𝗮𝗺𝘀𝗮𝘄𝗮 𝗱𝗮𝘀𝗵𝗶. 𝗛𝗮𝗻𝗻𝘂𝗻 𝘁𝗮 𝗱𝗮𝘂𝗸𝗲 𝗱𝗮𝗴𝗮 𝗸𝗮𝗻𝘁𝗮,𝘁𝗮 𝘀𝗮𝗻𝘆𝗮 𝗵𝗮𝗻𝗻𝘂𝘄𝗮𝗻𝘁𝗮 𝗱𝘂𝗸𝗸𝗮 𝗯𝗶𝘆𝘂𝗻 𝘁𝗮 𝗱𝗮𝗴𝗼𝘁𝗮 𝘁𝗮𝗻𝗮 𝗳𝘂𝘀𝗸𝗮𝗻𝘁𝗮𝗿𝘁𝗮 "𝗧𝗮𝘀𝗵𝗶 𝗸𝗶 𝘄𝘂𝗰𝗲 𝗴𝗶𝗱𝗮𝗻𝗸𝗶......𝗱𝗮𝗴𝗮 𝗻𝗮𝗻 𝗸𝘂 𝗸𝗮𝗶𝘁𝗮 𝗴𝗶𝗱𝗮𝗻𝘁𝗮 𝗸𝗮𝗶 𝘁𝘀𝗮𝘆𝗲......𝗱𝗮𝗴𝗮 𝗯𝗮𝘆𝗮 𝗱𝗮 𝗸𝗮𝗻𝘀𝗵𝗶 𝘆𝗮 𝗿𝗮𝗸𝗮𝘁𝗮 𝗶𝗻𝗱𝗮 𝘆𝗮 𝗱𝗮𝗰𝗲 𝘁𝗮𝗷𝗲 𝗱𝗶𝗻.....𝗸𝗶𝗻𝗷𝗶 𝗱𝘂𝗸𝗸𝗮 𝗯𝗮𝘆𝗮𝗻𝗮𝗶𝗻𝗮 𝗸𝗼?" 𝗦𝗮𝗺𝘂𝗻 𝗸𝗮𝗻𝘁𝗮 𝘁𝗮𝘆𝗶 𝗱𝗮 𝗴𝘆𝗮𝗱𝗮 𝗺𝗮𝘁𝗮 𝗸𝗮𝗶 𝗱𝗮 𝘄𝗮𝗻𝗶 𝗶𝗿𝗶𝗻 𝗺𝘂𝗴𝘂𝗻 𝘀𝗮𝗻𝘆𝗶𝗻 𝗷𝗶𝗸𝗶 𝗱𝗮 𝗯𝗮𝘁𝗮 𝘁𝗮𝗯𝗮 𝗷𝗶𝗻 𝗶𝗿𝗶𝗻𝘀𝗮 𝗯𝗮,𝘀𝗮𝗶𝘁𝗮 𝗷𝗮𝘄𝗼𝘁𝗮 𝘁𝗮 𝗿𝘂𝗻𝗴𝘂𝗺𝗲𝘁𝗮 𝘁𝗮𝗻𝗮 𝘀𝗮𝗸𝗲 𝘀𝗮𝗸𝗲 𝗺𝗮𝘁𝗮 𝘄𝗮𝘀𝘂 𝗮𝗱𝗱𝘂'𝗼'𝗶𝗻,𝗮𝗯𝗶𝗻𝗱𝗮 𝘆𝗮 𝘀𝗮𝗻𝘆𝗮 𝘁𝗮𝗷𝗶 𝗸𝗮𝗻𝘁𝗮 𝘆𝗮𝘆𝗶 𝘄𝗮𝗻𝗶 𝗶𝗿𝗶𝗻 𝘀𝗮𝗿𝗮𝘄𝗮,𝘁𝗮𝗸𝗲 𝗰𝗶𝘄𝗼𝗻 𝗸𝗮𝗶 𝘆𝗮 𝘀𝗮𝘂𝗸𝗮𝗿 𝗺𝗮𝘁𝗮. 𝗦𝗮𝘂𝗸𝗲 𝗹𝗮𝗯𝘂𝗹𝗲 𝗮𝗺𝗻𝗮 𝘁𝗮𝘆𝗶 𝗮 𝗸𝗮𝗿𝗼 𝗻𝗮 𝗯𝗮𝗯𝘂 𝗮𝗱𝗮𝗱𝗶,𝘀𝗮𝗻𝗻𝗮𝗻 𝘁𝗮 𝗺𝗮𝗶𝗱𝗮 𝗱𝘂𝗯𝗮𝗻𝘁𝗮 𝗸𝗮𝗻 𝗮𝗻𝗻𝗶 𝘁𝗮𝗻𝗮 𝗻𝗮𝗿𝗸𝗲 𝗳𝘂𝘀𝗸𝗮 𝗸𝗮𝗺𝗮𝗿 𝘇𝗮𝘁𝗮 𝘀𝗮𝗸𝗶 𝗸𝘂𝗸𝗮 "𝗔𝗻𝗻𝗶 𝗱𝗮𝗿𝗲 𝗳𝗮 𝘆𝗮 𝗿𝗶𝗴𝗮 𝘆𝗮𝘆𝗶,𝗵𝗮𝗿 𝘆𝗮𝗻𝘇𝘂 𝗯𝗮𝘀𝘂 𝘀𝗵𝗶𝗴𝗼 𝗱𝗮 𝗶𝘁𝗮 𝗯𝗮.....𝗸𝘂𝗺𝗮 𝘆𝗮𝗮 𝗺𝘂𝘀𝗮𝗱𝗱𝗶𝗾 𝘆𝗮𝗰𝗲 𝘀𝘂𝗻 𝘀𝗵𝗶𝗴𝗮 𝘄𝗮𝗷𝗲𝗻 𝗺𝗮𝗮𝗺𝗮𝗵....𝗱𝗮𝗴𝗮 𝗰𝗮𝗻 𝗸𝘂𝗺𝗮 𝘀𝗮𝗶 𝗻𝗮𝗻". 𝗔 𝗻𝘂𝘁𝘀𝗲 𝗮𝗻𝗻𝗶 𝘁𝗮 𝗱𝗮𝗴𝗮 𝗸𝗮𝗻𝘁𝗮 𝗱𝗮𝗴𝗮 𝘇𝗮𝗿𝗲 𝘄𝗮𝗿𝘄𝗮𝗿𝗮𝘆𝗲𝗻 𝗵𝗮𝗻𝗻𝘂𝗻𝘁𝗮 𝗱𝗮 𝘁𝗮𝗸𝗲𝘆𝗶 𝘁𝗮 𝗺𝗮𝗶𝗱𝗮 𝗸𝗮𝗻 𝗮𝗺𝗻𝗮 "𝗠𝗲 𝗸𝗶𝗸𝗲 𝗰𝗶 𝗻𝗲 𝗻𝗮 𝗯𝗮𝗸𝗮 𝘆𝗮𝗻𝗮 𝘇𝘂𝗯𝗮 𝗮𝗺𝗻𝗮?,𝗰𝗶 𝗱𝗮 𝘇𝘂𝗰𝗶?,𝘆𝗮𝘆𝗮𝗿𝗸𝗶 𝗰𝗲 𝗳𝗮?,𝗵𝗮𝗿 𝘀𝗮𝗶 𝗸𝗶𝗻 𝗴𝗮𝗷𝗶 𝗱𝗮 𝗴𝗮𝗻𝗶𝗻𝘁𝗮 𝘄𝗮𝘁𝗮𝗿𝗮𝗻𝗮.....𝘄𝗮𝘁𝗮𝗾𝗶𝗹𝗮 𝗱𝗮𝗿𝗲 𝗻𝗲 𝘆𝗮𝘆𝗶 𝗺𝘂𝘀𝘂 𝘀𝘂𝗸𝗮 𝘄𝘂𝗰𝗲 𝗱𝗮 𝗶𝘁𝗮,𝗮𝗺𝗺𝗮 𝗸𝗼𝗺𝗮 𝗺𝗲𝘆𝗲 𝗻𝗮𝘀𝗮𝗻 𝗵𝗮𝗺𝗺𝗮𝗻𝗸𝘂 𝘇𝗮𝗶 𝗸𝗮𝘄𝗼𝘁𝗮 𝘁𝗮𝗯𝗯𝗮𝘀 𝗸𝗼𝗱𝗮 𝗱𝗮𝗴𝗮 𝗯𝗮𝘆𝗮 𝗻𝗲" . 𝗧𝗮𝘆𝗶 𝗺𝗮𝗴𝗮𝗻𝗮𝗿 𝗰𝗶𝗸𝗶𝗻 𝘀𝗼𝗻 𝗸𝗮𝘄𝗮𝗿𝘄𝗮 𝗱𝗮 𝗮𝗺𝗻𝗮 𝘁𝘂𝗻𝗮𝗻𝗶𝗻 𝗸𝗼𝗺𝗮𝗶,𝗱𝘂𝗸 𝗱𝗮 𝗶𝘁𝗮𝗺𝗮 𝘁𝗮𝘀𝗼 𝗾𝘄𝗮𝗿𝗮𝗶 𝗮 𝘀𝗵𝗶𝗴𝗼 𝗱𝗮 𝗶𝘁𝗮𝗻,𝗱𝗼𝗻 𝗮𝗸𝘄𝗮𝗶 𝗺𝗮𝗴𝗮𝗻𝗴𝗮𝗻𝘂 𝗺𝗮𝘀𝘂 𝘆𝗮𝘄𝗮 𝗱𝗮 𝘁𝗮𝗸𝗲𝘀𝗼 𝘁𝗮𝘆𝗶 𝗱𝗮 𝗶𝘁𝗮. "𝗔𝗺𝗺𝗮 𝗮𝗻𝗻𝗶 𝘆𝗮𝘂𝘀𝗵𝗲?,𝗻𝗶 𝗸𝗼 𝗴𝗼𝗯𝗲 𝗻𝗲 𝗴𝗮𝗻𝗶 𝗻𝗮𝗸𝗲𝘆𝗶 𝘁𝗮𝘆𝗶 𝗻𝗶𝘀𝗮" "𝗦𝗮𝗶 𝗸𝗶𝘆𝗶 𝗳𝗶𝗳𝗳𝗶𝗸𝗲 𝗸𝗶𝗷𝗲 𝗮𝗶 𝘀𝗮𝗿𝗸𝗶𝗻 𝗴𝗮𝗿𝗮𝗷𝗲" 𝗦𝗮𝗱𝗱𝗶𝗾 𝗱𝗮𝗸𝗲 𝘀𝗵𝗶𝗴𝗼𝘄𝗮 𝗿𝗶𝗾𝗲 𝗱𝗮 𝗹𝗲𝗱𝗮 𝗮 𝗵𝗮𝗻𝗻𝘂𝗻𝘀𝗵𝗶 𝗱𝗮𝗸𝗲 𝗱𝗮𝘂𝗸𝗲 𝗱𝗮 𝘁𝗮𝗺𝗯𝗮𝗿𝗶𝗻 𝘄𝗮𝗻𝗶 𝗯𝗮𝗯𝗯𝗮𝗻 𝗸𝗮𝗺𝗳𝗮𝗻𝗶 𝗱𝗮 𝘆𝗮𝘆𝗶 𝘀𝗵𝘂𝗵𝘂𝗿𝗮 𝘄𝗮𝗷𝗲𝗻 𝗳𝗶𝗱𝗱𝗮 𝘀𝘂𝘁𝘂𝗿𝘂 𝗻𝗮 𝗺𝗮𝗻𝘆𝗮𝗻 𝗺𝘂𝘁𝗮𝗻𝗲. 𝗝𝘂𝘆𝗮𝘄𝗮 𝘁𝗮𝘆𝗶 𝘁𝗮 𝗱𝘂𝗯𝗲𝘀𝗵𝗶 𝘁𝗮𝗻𝗮 𝘀𝗮𝗸𝗲 𝗯𝗮𝘁𝗮 𝗿𝗮𝗶,𝘀𝗮𝗶 𝘁𝗮 𝘁𝘀𝘂𝗸𝗲 𝗯𝗮𝗸𝗶 𝗸𝗮𝘄𝗮𝗶 𝘁𝗮 𝗸𝗼𝗺𝗮 𝘁𝗮 𝘇𝗮𝘂𝗻𝗮 𝗯𝗮 𝘁𝗮𝗿𝗲 𝗱𝗮𝘁𝗮 𝘀𝗮𝗸𝗲 𝗰𝗲𝘄𝗮 𝗸𝗼𝗺𝗮𝗶 𝗯𝗮,𝗱𝗼𝗻 𝘁𝗮 𝘀𝗮𝗻 𝗺𝘂𝗱𝗱𝗶𝗻 𝘁𝗮𝗰𝗲 𝘇𝗮𝘁𝗮 𝘀𝗮𝗸𝗲 𝗺𝗮𝗴𝗮𝗻𝗮𝗿 𝘇𝗮𝘀𝘂 𝘆𝗶𝘁𝗮 𝘀𝗮'𝗶𝗻𝘀𝗮 𝗻𝗲 𝗸𝗮𝘄𝗮𝗶 𝗱𝗮 𝘀𝗮𝗱𝗱𝗶𝗾,𝗱𝗮𝗴𝗮 𝗾𝗮𝗿𝘀𝗵𝗲 𝘆𝗮 𝘀𝗮𝗸𝗮𝘁𝗮 𝗸𝘂𝗸𝗮. "𝗔𝗻𝗻𝗶 𝗸𝗲𝘆 𝗻𝗮 𝘀𝗮𝘀𝘀𝗮𝗻 𝗕𝗕 𝗳𝗮𝗿𝗼𝘂𝗾,𝘆𝗮𝗰𝗲 𝗻𝗮 𝘀𝗮𝗸𝗮 𝗺𝘂𝘀𝘂 𝗸𝗮𝘆𝗮𝗻 𝗻𝗮𝗻 𝗮 𝗰𝗶𝗸𝗶,𝗵𝗮𝗺𝗺𝗮 𝘇𝗮𝗶𝘇𝗼 𝘆𝗮 𝘀𝗵𝗶𝗿𝘆𝗮". 𝗪𝗮𝗶𝘄𝗮𝘆𝗮𝘄𝗮 𝘁𝗮𝘆𝗶 𝘁𝗮𝗻𝗮 𝗯𝗮𝘄𝗮 𝗮𝗺𝗻𝗮 𝘂𝗺𝗮𝗿𝗻𝗶 𝘁𝗮𝗻𝗮 𝗺𝗮𝘁𝗮 𝗻𝘂𝗻𝗶 𝗱𝗮 𝗶𝗻𝗱𝗮 𝘁𝗮 𝗮𝗷𝗶𝘆𝗲𝘀𝗵𝗶. "𝗕𝗮 𝗶𝗻𝗱𝗮 𝘇𝗮𝗸𝗮𝗷𝗲 𝗳𝗮 𝘀𝗮𝗶𝗸𝗮 𝗸𝗮𝗺𝗺𝗮𝗹𝗮 𝘀𝗵𝗶𝗿𝘆𝗮𝘄𝗮 𝗻𝗮 𝗿𝗮𝗸𝗮𝗸𝗮 𝗸𝗮 𝘆𝗶𝘄𝗮 𝗮𝗻𝗻𝗶 𝘀𝗮𝗹𝗹𝗮𝗺𝗮......𝗱𝗼𝗻 𝗯𝗮 𝘇𝗮𝗸𝗮 𝗵𝗮𝗻𝗮𝗻𝗶 𝗸𝘄𝗮𝗻𝗰𝗶𝘆𝗮 𝗱𝗮 𝘄𝘂𝗿𝗶 𝗯𝗮 𝘆𝗮𝘂......𝘆𝗮𝗱𝗱𝗮 𝗻𝗮 𝗴𝗮𝗷𝗶 𝗱𝗶𝗻𝗻𝗮𝗻 𝗯𝗮𝗰𝗰𝗶 𝗻𝗮𝗸𝗲 𝗯𝘂𝗾𝗮𝘁𝗮 𝗺𝗲 𝘁𝘀𝗮𝗵𝗼.....𝗸𝗼 𝗳𝗮𝗻𝗻𝗮 𝗵𝗶𝗱𝗶𝗺𝗮𝗿𝗸𝗮 𝘁𝗮 𝗵𝗮𝗻𝗮𝗺𝗶𝗻 𝗷𝗶𝗻 𝗺𝘂𝗿𝘆𝗮𝗿𝘁𝗮" 𝗙𝗮𝗿𝗼𝘂𝗾 𝗱𝗮𝘆𝗮 𝗿𝗶𝗾𝗼 𝗳𝘂𝗮𝗱 𝘄𝗮𝗻𝗱𝗮 𝗸𝗲 𝗾𝗼𝗾𝗮𝗿𝗶𝗻 𝘄𝘂𝗰𝗲𝘄𝗮 𝗸𝗮𝗶 𝘁𝘀𝗮𝘆𝗲 𝗰𝗶𝗸𝗶𝗻 𝗴𝗶𝗱𝗮𝗻 𝘆𝗮 𝗳𝗮𝗱𝗮. 𝗪𝗮𝗶𝘄𝗮𝘆𝗼𝘄𝗮 𝘆𝗮𝘆𝗶 𝘆𝗮 𝗸𝗮𝗹𝗹𝗶 𝗳𝗮𝗿𝗼𝘂𝗾 𝗱𝗶𝗻 "𝗗𝘂𝗸𝗮 𝗸𝗮𝗶 𝗸𝗮𝘀𝗼.....𝗸𝗮 𝗮𝘇𝗮𝗺𝗮 𝗸𝗮𝗻𝗸𝗮 𝗵𝗶𝗱𝗶𝗺𝗮𝗿 𝗱𝗮 𝗸𝘄𝗮𝘁𝗮 𝗸𝘄𝗮𝘁𝗮 𝗯𝗮𝘁𝗮 𝗱𝗮 𝘄𝗮𝗻𝗶 𝘁𝘂𝘀𝗵𝗲 𝗸𝗼 𝗸𝘂𝗺𝗮 𝗮𝗺𝗳𝗮𝗻𝗶.....𝘄𝗮𝗶 𝘄𝗮𝗶𝘁 𝗺𝗮......𝘁𝘂𝗸𝘂𝗻𝗻𝗮 𝗸𝗮𝗻𝗮 𝗻𝘂𝗳𝗶𝗻 𝗻𝗶 𝘇𝗮𝗸𝗮 𝘀𝗮𝗸𝗮 𝗮 𝗴𝗮𝗯𝗮 𝗸𝗮𝗸𝗮𝗶 𝗰𝗮𝗻 𝗴𝗶𝗱𝗮𝗻?" "𝗪𝗮𝗹𝗹𝗮𝗵𝗶 𝘄𝗮𝗹𝗹𝗮𝗵𝗶 𝘀𝗮𝗶𝗸𝗮 𝘀𝗵𝗶𝗿𝘆𝗮 𝗸𝗮𝗺𝗮𝗻 𝗸𝗼𝘄𝗮𝗻𝗻𝗲 𝗮𝗻𝗴𝗼,𝗸𝘂𝗺𝗮 𝘀𝗮𝗶𝗻𝗮 𝗸𝗮𝗶𝗸𝗮 𝗵𝗮𝗿 𝗰𝗶𝗸𝗶" 𝗬𝗮𝘆𝗶 𝗴𝗮𝗴𝗴𝗮𝘄𝗮𝗿 𝘆𝗮𝗻𝗸𝗮𝗿 𝗺𝗮𝘀𝗮 𝗯𝗮𝘆𝗮 𝗱𝗮 𝗿𝗮𝗻𝘁𝘀𝘂𝘄𝗮,𝗱𝗼𝗻 𝗿𝗮𝗻𝘁𝘀𝘂𝘄𝗮𝗿 𝗰𝗲 𝗸𝗮𝗱𝗮𝗶 𝘆𝗮𝘀𝗮𝗻 𝘇𝗮𝘁𝗮 𝘀𝗮𝗸𝗮 𝗳𝘂𝗮𝗱 𝘆𝗮𝘆𝗶 𝗮𝗯𝗶𝗻𝗱𝗮 𝘆𝗮𝗸𝗲𝘀𝗼 𝗱𝗶𝗻 𝗯𝗮 𝘁𝗮𝗿𝗲 𝗱𝗮 𝗷𝗮𝗻 𝘇𝗮𝗻𝗰𝗲 𝗯𝗮,𝗸𝗮𝘀𝗮𝗻𝗰𝗲𝘄𝗮𝗿 𝗱𝘂𝗸 𝘄𝗮𝗻𝗱𝗮 𝘆𝗮𝘆𝗶 𝗿𝗮𝗻𝘁𝘀𝘂𝘄𝗮 𝗮 𝗰𝗶𝗸𝗶𝗻 𝘀𝘂 𝘆𝗮𝗻𝗮 𝗾𝗼𝗾𝗮𝗿𝗶𝗻 𝗳𝗶𝗱𝗱𝗮 𝗱𝗮𝗻 𝘂𝘄𝗮𝗻𝘀𝗮 𝗱𝗮𝗴𝗮 𝗿𝗮𝗻𝘁𝘀𝘂𝘄𝗮𝗿. 𝗜𝗱𝗮𝗻𝘂 𝘆𝗮 𝘇𝘂𝗯𝗮 𝗺𝗮𝘀𝗮,𝗸𝗮𝗺𝗮𝗿 𝘇𝗮𝗶𝘆𝗶 𝗺𝗮𝗴𝗮𝗻𝗮 𝘀𝗮𝗶 𝗸𝘂𝗺𝗮 𝘆𝗮 𝗳𝗮𝘀𝗮,𝘆𝗮 𝗷𝘂𝘆𝗮 𝘇𝘂𝘄𝗮 𝘀𝗮𝘀𝗵𝗲𝗻 𝗳𝗮𝗿𝗼𝘂𝗾 𝗱𝗶𝗻 𝘆𝗮𝗻𝗮 𝘁𝗮𝗸𝗮𝘄𝗮 𝗰𝗶𝗸𝗶𝗻 𝗻𝘂𝘁𝘀𝘂𝘄𝗮𝗿 𝗻𝗮𝗻 𝘁𝗮𝘀𝗮. 𝗖𝗮𝗸 𝘆𝗮 𝘁𝘀𝗮𝘆𝗮 𝗱𝗮𝗯 𝗱𝗮 𝘇𝗮𝗶 𝘀𝗵𝗶𝗴𝗮,𝗺𝘂𝗿𝗺𝘂𝘀𝗵𝗶 𝗺𝗲 𝗾𝗮𝗿𝗮𝗺𝗶𝗻 𝘀𝗮𝘂𝘁𝗶 𝘆𝗮 𝘀𝘂𝗯𝘂𝗰𝗲 𝗺𝗮𝘀𝗮,𝘆𝗮 𝘄𝗮𝗶𝘄𝗮𝘆𝗮 𝘆𝗮 𝗱𝘂𝗯𝗶 𝗳𝗮𝗿𝗼𝘂𝗾 𝗱𝗶𝗻 "𝗪𝗮𝗹𝗹𝗮𝗵𝗶 𝘆𝗮𝗿𝗼𝗻 𝗻𝗮𝗻 𝗸𝗮 𝗿𝗮𝗶𝗻𝗮𝗻𝗶 𝗱𝗮 𝘆𝗮𝘄𝗮,𝘄𝗮𝗶 𝗸𝗮 𝗺𝗮𝗻𝘁𝗮 𝗸𝘄𝗮𝗻𝗮 𝗱'𝗮𝗶 𝗱'𝗮𝗶 𝗵𝗮𝗿 𝗯𝗮𝗸𝘄𝗮𝗶 𝗻𝗮 𝗯𝗮𝗸𝗮.....𝘁𝘂𝗸𝘂𝗻𝗻𝗮 𝗺𝗮 𝘄𝗮𝗶 𝘄𝗮𝘆𝗲 𝘆𝗮𝗰𝗲 𝗺𝗮𝗸𝗮 𝗵𝗮𝗸𝗮 𝗻𝗮 𝘁𝘀𝗮𝗿𝗮 𝗸𝗼𝗺𝗮𝗶 𝗻𝗲?,𝗮𝘂𝗿𝗲𝗻 𝗱𝗮𝗻𝗮 𝘁𝘀𝗮𝗿𝗮 𝗱𝗮𝗴𝗮 𝗱𝗮𝘂𝗿𝗮𝘄𝗮 𝘀𝗮𝗶 𝗿𝗮𝗸𝗮𝘁𝗮 𝗴𝗶𝗱𝗮𝗻 𝘁𝗮𝗿𝗯𝗶𝘆𝘆𝗮 𝗱𝗮 𝘇𝗮𝘀𝘂𝘆𝗶?" "𝗚𝗶𝗱𝗮𝗻 𝘁𝗮𝗿𝗯𝗶𝘆𝘆𝗮?" 𝗙𝗮𝗿𝗼𝘂𝗾 𝗱𝗶𝗻 𝘆𝗮 𝗳𝗮𝗱𝗮 𝘆𝗮𝗻𝗮 𝗱𝗮𝗻𝗻𝗲 𝗱𝗮𝗿𝗶𝘆𝗮𝗿𝘀𝗮,𝗱𝗼𝗻 𝘁𝘂𝗻 𝗱𝗮𝗴𝗮 𝗻𝗮𝗻 𝗵𝗮𝗿 𝘀𝗮𝗻𝗱𝗮 𝘇𝗮𝗶 𝗯𝗮𝗿𝗼 𝗳𝘂𝗮𝗱 𝗱𝗶𝗻 𝗰𝗶𝗸𝗶𝗻 𝗴𝗶𝗱𝗮𝗻𝘀𝗮 𝗯𝗮𝘆𝗮𝘀𝗼𝗻 𝘆𝗮𝗴𝗮 𝘄𝗮𝗻𝗶 𝗮𝗯𝘂 𝗺𝗲 𝗸𝗮𝗺𝗮 𝗱𝗮 𝘄𝗮𝘀𝗮 𝘀𝗮𝗺.....𝘆𝗮𝗻𝗮𝘀𝗼𝗻 𝗶𝗱𝗮𝗻𝗺𝗮 𝘆𝗮𝗻𝗮 𝗱𝗮𝘂𝗸𝗮𝗻 𝗮𝗯𝘂𝗻 𝗮 𝗺𝗮𝘇𝗮𝘂𝗻𝗶𝗻 𝘄𝗮𝘀𝗮 𝘀𝗼 𝘆𝗮𝗸𝗲 𝘆𝗮𝗷𝗶 𝘀𝗼𝘀𝗮𝗶 𝗮 𝗿𝗮𝗻𝘀𝗮 𝗮𝘂𝗿𝗲 𝘆𝗮𝘆𝗶 𝗸𝗮𝗺𝗮𝗿 𝗸𝗼𝘄𝗮𝗻𝗻𝗲 𝗺𝗮𝗴𝗶𝗱𝗮𝗻𝗰𝗶. "𝗧𝗼 𝗸𝗮 𝘀𝗮𝗯𝗮 𝗹𝗶𝘀𝘀𝗮𝗳𝗶 𝘆𝗮𝗹𝗹𝗮𝗯𝗮𝗶" 𝗬𝗮 𝗳𝗮𝗱𝗮 𝘁𝗮𝗻𝗮 𝗷𝗮𝗻 𝗵𝗮𝗻𝗻𝘂𝗻𝘀𝗮 𝘀𝘂𝗻𝗮 𝗾𝗮𝗿𝗮𝘀𝗮𝘄𝗮 𝗰𝗶𝗸𝗶. 𝗗𝗮𝗴𝗮 𝗾𝗮𝗿𝘀𝗵𝗲 𝗱𝗮𝗶 𝗱𝗼𝗹𝗲 𝗶𝗱𝗮𝗻𝘂 𝘆𝗮 𝘇𝘂𝗯𝗮𝘄𝗮 𝗳𝗮𝗿𝗼𝘂𝗾 𝗱𝗶𝗻,𝘆𝗮𝘆𝗶 𝘄𝗮𝗻𝗸𝗮 𝗱𝗼𝗻 𝗱𝗮𝗺𝗮 𝘀𝗮𝗯𝗼𝗻𝘀𝗵𝗶 𝗻𝗲 𝗱𝘂𝗸 𝗱𝗮𝗿𝗲,𝗯𝗮𝗿𝗲 𝘆𝗮𝘂 𝗱𝗶𝗻 𝗱𝗮 𝘀𝘂𝗸𝗮 𝘄𝘂𝗻𝗶 𝘇𝗶𝗿𝗴𝗮 𝘇𝗶𝗿𝗴𝗮𝗿 𝗱𝗮 𝗯𝗮𝗯𝘂 𝗴𝗮𝗶𝗿𝗮 𝗯𝗮𝗿𝗲 𝗱𝗮𝗹𝗶𝗹𝗶 𝗱𝗮 𝗳𝗮𝗿𝗼𝘂𝗾 𝘆𝗮 𝗮𝘇𝗮 𝗺𝗮𝘀𝗮. 𝗬𝗮𝗷𝗶 𝗱𝗮𝗱𝗶𝗻 𝗷𝗶𝗸𝗶𝗻𝘀𝗮 𝘀𝗼𝘀𝗮𝗶,𝗳𝗮𝗿𝗼𝘂𝗾 𝘆𝗮 𝗳𝗶𝗱𝗱𝗼 𝗺𝗮𝘀𝗮 𝗸𝗼𝗺𝗮𝗶. 𝗞𝗮𝗺𝗮𝗻 𝗱𝗮𝘇𝘂 𝗵𝗮𝗸𝗮 𝘆𝗮 𝗱𝗶𝗻𝗴𝗮 𝗺𝗶𝗾𝗮 𝗺𝗮𝘀𝗮 𝗸𝗼𝗺𝗮𝗶 𝘆𝗮𝗻𝗮 𝘀𝗵𝗶𝗿𝘆𝗮𝘄𝗮,𝘀𝗮𝗶 𝗴𝗮𝘀𝗵𝗶 𝘆𝗮 𝗳𝗶𝘁𝗼 𝗳𝗲𝘀 𝗰𝗶𝗸𝗶𝗻 𝗼𝗹𝗶𝘃𝗲 𝗰𝗼𝗹𝗼𝗿,𝘆𝗮𝘆𝗶 𝗮𝗺𝗳𝗮𝗻𝗶 𝗱𝗮 𝗵𝘂𝗹𝗮 𝗱𝗮 𝗵𝗮𝗹𝗳 𝗰𝗼𝘃𝗲𝗿 𝘀𝗵𝗼𝗲 𝗱𝘂𝗸𝗮 𝗸𝗮𝗹𝗮𝗻 𝗽𝗮𝗹𝗲 𝘀𝗮𝗴𝗲 𝗱𝗮𝘆𝗮 𝗱𝗮𝗰𝗲 𝗾𝘄𝗮𝗿𝗮𝗶 𝗱𝗮 𝗼𝗹𝗶𝘃𝗲 𝗰𝗼𝗹𝗼𝗿 𝗱𝗶𝗻 𝗱𝗮 𝘄𝗮𝗻𝗶 𝗶𝗿𝗶𝗻 𝗺𝗮𝘁𝗰𝗵𝗶𝗻𝗴. 𝗗𝗮𝗴𝗮 𝘀𝗵𝗶 𝗵𝗮𝗿 𝗳𝗮𝗿𝗼𝘂𝗾 𝘀𝘂𝗻𝘆𝗶 𝘄𝗮𝗻𝗶 𝗯𝗮𝗹𝗮'𝗶𝗻 𝗾𝘄𝗮𝗿𝗲𝘄𝗮 𝘄𝗮𝗷𝗲𝗻 𝗶𝘆𝗮 𝗵𝗮𝗱𝗮 𝗰𝗼𝗹𝗼𝗿 𝗱𝗮 𝘀𝗮𝗻𝘆𝗮 𝘀𝘂𝘁𝘂𝗿𝗮𝗿 𝗱𝗮 𝘇𝗮𝘁𝗮 𝘇𝗮𝘂𝗻𝗮 𝗮 𝗷𝗶𝗸𝗶. 𝗗𝘂𝗸 𝗱𝗮 𝗮 𝘆𝗮𝗻𝘇𝘂 𝘀𝗵𝗶 𝗯𝗮𝗶𝗱𝗮 𝘄𝗮𝗻𝗻𝗮𝗻 𝗹𝗼𝗸𝗮𝗰𝗶𝗻,𝗱𝗼𝗻 𝘆𝗮𝗻𝗮 𝗱𝗮 𝗽𝗿𝗼𝗳𝗲𝘀𝘀𝗶𝗼𝗻𝗮𝗹 𝗰𝗹𝗼𝘀𝗲𝘁 𝗼𝗿𝗴𝗮𝗻𝗶𝘀𝗲𝗿 𝗱𝗮𝗸𝗲 𝘁𝘀𝗮𝗿𝗮 𝗺𝗮𝘀𝗮 𝗸𝗮𝘆𝗮𝗻 𝗱𝗮 𝘇𝗮𝗶𝘆𝗶 𝗮𝗺𝗳𝗮𝗻𝗶 𝗱𝗮𝘀𝘂 𝗻𝗮 𝘁𝘀𝗮𝗵𝗼𝗻 𝘀𝗮𝘁𝗶𝘁𝘁𝗶𝗸𝗮,𝘄𝗮𝗻𝗱𝗮 𝘆𝗮 𝗮𝗷𝗶𝘆𝗲𝘀𝘂 𝗻𝗲 𝗮 𝗱𝘂𝗸𝗮 𝗴𝘂𝗿𝗮𝗿𝗲𝗻 𝗱𝗮 𝘆𝗮𝗸𝗮𝗻 𝗶𝘆𝗮 𝘇𝘂𝘄𝗮 𝘆𝗮𝘆𝗶 𝘀𝗮𝘁𝗶 𝗸𝗼 𝘀𝗮𝗺𝗮 𝗱𝗮 𝗵𝗮𝗸𝗮,𝗸𝗼𝘄𝗮𝗻𝗻𝗲 𝗸𝘂𝗺𝗮 𝗮𝗹𝗯𝗮𝘀𝗵𝗶𝗻𝘀𝗮 𝗱𝗮𝗯𝗮𝗻 𝗸𝗼𝗱𝗮 𝘆𝗮𝘆𝗶 𝘄𝗮𝘁𝗮𝗻𝗻𝗶 𝗯𝗮𝗶𝘆𝗶 𝗮𝗶𝗸𝗶𝗻𝘀𝗮 𝗯𝗮. 𝗦𝗮𝗶𝗱𝗮𝗶 𝗱𝘂𝗸 𝗱𝗮 𝗵𝗮𝗸𝗮 𝗱𝘂𝗸 𝗿𝗮𝗻𝗱𝗮 𝘆𝗮 𝘀𝗮𝗺𝘂 𝗸𝗮𝗻𝘀𝗮 𝘆𝗮 𝗵𝗮𝗱𝗮𝘄𝗮 𝗸𝗮𝗻𝘀𝗮 𝗱𝗿𝗲𝘀𝘀𝗶𝗻𝗴 𝘁𝗮 𝗳𝗮𝗿𝗮𝘁 𝗱𝗮𝘆𝗮 𝗳𝗮𝗿𝗼𝘂𝗾 𝗸𝗲 𝗴𝗮𝗻𝗲𝘄𝗮. 𝗬𝗮𝗮𝗮𝗻 𝗵𝗮𝗹𝗶𝗻𝘀𝗮,𝗺𝗮𝘆𝗲 𝗻𝗲 𝘄𝗮𝗷𝗲𝗻 𝗶𝘆𝗮 𝘁𝘀𝗮𝗿𝗮𝘄𝗮 𝗷𝗶𝗸𝗶 𝗮𝗱𝗼 𝗱𝗮 𝘆𝗮𝘄𝗮𝗻𝗰𝗶 𝘆𝗮𝗸𝗲 𝘀𝗮𝗸𝗲 𝘁𝗮𝗸𝗮 𝗺𝘂𝗵𝗶𝗺𝗺𝗶𝘆𝗮𝗿 𝗿𝗮𝘄𝗮 𝘄𝗮𝗷𝗲𝗻 𝗳𝘂𝘀𝗴𝗮𝗿 𝗵𝗮𝗻𝗸𝘂𝗹𝗮𝗻 '𝘆𝗮𝗺𝗺𝗮𝘁𝗮𝗻 𝗱𝗮𝗸𝗲 𝗾𝘂𝗹𝗮𝗳𝘂𝗰𝗶𝗻𝘀𝗮. "𝗠𝗮 𝘀𝗵𝗮 𝗔𝗹𝗹𝗮𝗵.... .𝗽𝗲𝗿𝗳𝗲𝗰𝘁 𝗺𝗮𝘁𝗰𝗵" 𝗙𝘂𝗮𝗱 𝗱𝗶𝗻 𝘆𝗮 𝗳𝗮𝗱𝗶 𝘆𝗮𝗻𝗮 𝘀𝗵𝗮𝗳𝗮 𝗴𝗮𝗯𝗮𝗻 𝗯𝗮𝗯𝗯𝗮𝗻 𝗿𝗶𝗴𝗮𝗿 𝗱𝗮 𝘆𝗮𝘀𝗵𝗮 𝗮𝗶𝗸𝗶. 𝗦𝗵𝗶 𝗸𝗮𝗻𝘀𝗮 𝗳𝗮𝗿𝗼𝘂𝗾 𝗱𝗶𝗻 𝗸𝗮𝗹𝗹𝗼𝗻𝘀𝗮 𝘆𝗮𝗸𝗲,𝘆𝗮𝗱𝗱𝗮 𝗸𝗮𝘆𝗮𝗻 𝘀𝘂𝗸𝗮 𝗮𝗺𝘀𝗵𝗲𝘀𝗵𝗶 𝗺𝗮𝘁𝘂𝗾𝗮 𝘀𝘂𝗸𝗮 𝘀𝗮𝗸𝗲 𝘀𝘂𝗿𝗮 𝗱𝗮 𝗸𝘄𝗮𝗿𝗷𝗶𝗻𝗶𝗻 𝗱𝗮 𝗔𝗹𝗹𝗮𝗵 𝘆𝗮 𝗯𝗮𝘀𝗵𝗶. 𝗡𝗲𝗺𝗮𝗻 𝘄𝗮𝗷𝗲𝗻 𝘇𝗮𝗺𝗮 𝘆𝗮𝗴𝗮 𝘆𝗮𝗻𝗮𝘆𝗶,𝘀𝗮𝗶 𝘆𝗮𝘆𝗶 𝗯𝗮𝗻𝘇𝗮 𝗱𝗮𝘀𝗵𝗶,𝘆𝗮 𝗳𝗶𝗱𝗱𝗮 𝘄𝗮𝘆𝗮 𝘆𝗮 𝗸𝗶𝗿𝗮 𝗮𝗯𝗯𝗮..... "𝗔𝗯𝗯𝗮 𝗺𝘂𝗻 𝗴𝗮𝗺𝗮,𝗼𝗸𝗮𝘆 𝘁𝗼" 𝗠𝗮𝗶𝗱𝗮 𝘄𝗮𝘆𝗮𝗿 𝘆𝗮𝘆𝗶 𝗮𝗹𝗷𝗶𝗵𝘂𝗻𝘀𝗮 𝘆𝗮 𝗺𝗶𝗾𝗲 "𝗦𝗮𝗶𝗸𝗮 𝘁𝗮𝘀𝗼 𝗺𝘂𝗷𝗲 𝗮𝘆𝗶 𝗺𝗮𝗸𝗮 𝗳𝗮𝗱𝗮𝗻 𝗴𝗶𝗱𝗮𝗻 𝗮𝘂𝗿𝗲". 𝗬𝗮 𝗳𝘂𝗿𝘁𝗮 𝘆𝗮𝗻𝗮 𝗱𝗮𝗻𝗻𝗲 𝗱𝗮𝗿𝗶𝘆𝗮𝗿𝘀𝗮. 𝗗𝗮 𝗸𝗮𝗹𝗹𝗼 𝘆𝗮𝗯𝗶 𝗳𝗮𝗿𝗼𝘂𝗾 𝗱𝗶𝗻 𝗴𝗮𝗹𝗮𝗹𝗮 𝗸𝗮𝘄𝗮𝗶 𝘆𝗮𝗻𝗮 𝗱𝘂𝗯𝗮𝗻𝘀𝗮. "𝗞𝗮 𝗳𝗮𝗿𝗮 𝘄𝘂𝗰𝗲 𝗶𝘆𝗮𝗸𝗮𝗻𝗸𝗮 𝗳𝗮......𝗳𝗮𝗱𝗮 𝗰𝗲 𝗺𝗮𝗸𝗮 𝗮𝗸𝗮𝘆𝗶 𝗺𝘂𝗻 𝗿𝗮𝗯𝘂?" 𝗬𝗮 𝗳𝗮𝗱𝗮 𝘆𝗮𝗻𝗮 𝗷𝗶𝗳𝗮𝗻 𝗳𝗮𝗿𝗼𝘂𝗾 𝗱𝗮 𝗵𝗮𝗿𝗮𝗿𝗮 𝘄𝗮𝗻𝗱𝗮 𝘁𝘂𝗻𝗶 𝘆𝗮 𝗸𝗮𝗶 𝗾𝗼𝗳𝗮,𝗱𝗼𝗹𝗲 𝘆𝗮 𝗺𝗶𝗾𝗲 𝗵𝗮𝗿 𝗰𝗶𝗸𝗶𝗻 𝗿𝗮𝗻𝘀𝗮 𝘆𝗮𝗻𝗮 𝗷𝗶𝗻 𝗮𝗯𝘂𝗻 𝘆𝗮 𝗶𝘀𝗮 𝗵𝗮𝗸𝗮. 𝗦𝗵𝗶 𝘀𝗮𝗺 𝗯𝗮𝗶 𝗸𝗮𝘄𝗼 𝗵𝗮𝗸𝗮 𝗮𝗯𝘂𝗻 𝘇𝗮𝗶 𝗷𝘂𝘆𝗲 𝗯𝗮,𝗱𝗮 𝘁𝗮 𝘆𝗮𝘆𝗮 𝗺𝗮 𝘇𝗮𝗶 𝗯𝗮𝗿𝗶 𝗮𝘆𝗶 𝗵𝗮𝗸𝗮 𝗱𝗮𝘀𝗵𝗶?,𝘁𝗮𝗯𝗯𝗮𝘀 𝗱𝗮 𝗿𝗮𝗻𝗮𝗿 𝗱𝗮𝘆𝗮 𝗱𝗮𝘂𝗸𝗼 𝘄𝗮𝗻𝗰𝗮𝗻 𝘁𝘀𝗼𝗵𝗼𝗻 𝗻𝗮𝘁𝗮 𝘇𝗮𝗶 𝗸𝗶𝗿𝗮 𝗺𝗮'𝗮𝗶𝗸𝗮𝘁𝗮𝗻𝘀𝗮 𝘀𝘂 𝘀𝗵𝗮𝗶𝗱𝗮 𝗮 𝗱𝗮𝘂𝗿𝗮 𝗮𝘂𝗿𝗲𝗻 𝗮 𝘄𝗮𝗷𝗲𝗻 𝗮 𝘄𝘂𝗰𝗲 𝘄𝗮𝗷𝗲𝗻,𝘆𝗮 𝘁𝗮𝘁𝘁𝗮𝗿𝗮 𝘆𝗮𝘆𝗶 𝘁𝗮𝗳𝗶𝘆𝗮𝗿𝘀𝗮 𝘀𝗮𝗶 𝘀𝗮𝗻𝗱𝗮 𝘆𝗮 𝗴𝗮𝗺𝗮 𝘂𝘇𝘂𝗿𝗼𝗿𝗶𝗻𝘀𝗮 𝘁𝘂𝗸𝘂𝗻𝗻𝗮,𝗵𝗮𝗸𝗮 𝗸𝗮𝘄𝗮𝗶 𝗳𝗮𝗿𝗼𝘂𝗾 𝗱𝗶𝗻 𝘆𝗮𝘆𝗶 𝗿𝘂𝘄𝗮 𝗱𝗮 𝘁𝘀𝗮𝗸𝗶 𝘆𝗮 𝗺𝗮𝗶𝗱𝗮 𝗹𝗮𝗺𝗮𝗿𝗶𝗻 𝘄𝗮𝗻𝗶 𝘀𝗲𝗿𝗶𝗼𝘂𝘀. 𝗤𝘄𝗮𝗾𝘄𝗾𝘄𝗮𝗿𝗮𝗻 𝗺𝗼𝘁𝘀𝗶 𝗸𝗮𝘀𝗮 𝘆𝗮𝘆𝗶 𝘀𝗮𝗻𝗱𝗮 𝗮𝗯𝗯𝗮 𝘆𝗮𝗸𝗲 𝗺𝗮𝘀𝗮 𝗻𝗮𝘀𝗶𝗵𝗮 𝗴𝗮𝗺𝗶 𝗱𝗮 𝗸𝗮𝗿𝗮𝗻𝘁𝗮 𝗺𝗮𝘀𝗮 𝗵𝗮𝗹𝗮𝘆𝗲𝗻 𝗺𝗮𝘁𝗮 𝗱𝗮 𝘆𝗮𝗱𝗱𝗮 𝗮𝗸𝗲 𝘇𝗮𝗺𝗮 𝗱𝗮𝘀𝘂 𝗹𝗮𝗳𝗶𝘆𝗮,𝗸𝘂𝗻𝘆𝗮 𝗱𝗮 𝘁𝗮𝘂𝘀𝗮𝘆𝗶𝗻 𝗮𝗯𝗯𝗮𝗻 𝘆𝗮 𝗸𝗮𝗺𝗮𝘀𝗵𝗶 𝘆𝗮𝗱𝗱𝗮 𝘆𝗮𝗸𝗲 𝗯𝗮𝘆𝗮𝗻𝗶𝗻 𝗱𝗮 𝗴𝗮𝘀𝗸𝗲𝗻 𝗴𝗮𝘀𝗸𝗲. 𝗬𝗮 𝘀𝗮𝗻𝗶,𝗯𝗮𝘆𝗮𝗻𝗮𝗶 𝗻𝗲 𝗺𝗮𝘀𝘂 𝗮𝗺𝗳𝗮𝗻𝗶 𝗮𝗺𝗺𝗮 𝗳𝗮 𝗴𝗮 𝗺𝘂𝘁𝘂𝗺𝗶𝗻 𝗱𝗮 𝘆𝗮 𝗱𝗮𝘂𝗸𝗮 𝗱𝗮 𝗴𝗮𝘀𝗸𝗲𝗻 𝗴𝗮𝘀𝗸𝗲 𝗮𝘂𝗿𝗲 𝘆𝗮𝘆𝗶 𝗶𝗿𝗶𝗻 𝗻𝗮 𝗺𝘂𝘁𝗮𝗻𝗲.....𝗮𝘂𝗿𝗲 𝗸𝘂𝗺𝗮 𝘆𝗮𝘆𝗶 𝗶𝗿𝗶𝗻 𝗻𝗮 𝗸𝗼𝘄𝗮 𝗱𝗮 𝗸𝗼𝘄𝗮,𝗯𝗮𝘄𝗮𝗶.𝗺𝘂𝘁𝘂𝗺 𝗶𝗿𝗶𝗻𝘀𝗮 𝗱𝗮 𝗯𝗮𝗶𝗷𝗶𝗻 𝘀𝗵𝗶 𝗸𝗮𝗻𝘀𝗮 𝘆𝗮𝗻𝗮 𝗱𝗮 𝗰𝗶𝗸𝗮𝗸𝗸𝗲𝗻 𝗹𝗼𝗸𝗮𝗰𝗶𝗻 𝗸𝗮𝗻𝘀𝗮 𝗯𝗮 𝗯𝗮𝗿𝗲 𝗻𝗮 𝘄𝗮𝘁𝗮.....𝘄𝗮𝘁𝗮𝗻 𝗱𝗮 𝘆𝗮 𝗸𝗶𝗹𝗹𝗮𝗰𝗲𝘁𝗮 𝗻𝗲 𝗸𝗮𝘄𝗮𝗶 𝗱𝗼𝗻 𝘆𝗮 𝘀𝗮𝗶𝘁𝗮 𝗱𝗮𝗯𝗶'𝘂𝗻𝘁𝗮.......𝘆𝗮 𝗸𝘂𝗺𝗮 𝗻𝘂𝗻𝗮 𝗺𝗮𝘁𝗮 𝗴𝗶𝗿𝗺𝗮 𝗱𝗮 𝘆𝗮𝘄𝗮𝗻 𝗮𝗱𝗮𝗱𝗶𝗻 𝗸𝘂𝘀𝗸𝘂𝗿𝗲𝗻 𝗱𝗮𝘁𝗮 𝘁𝗮𝗳𝗸𝗮 𝗮 𝗿𝗮𝘆𝘂𝘄𝗮𝗿𝘁𝗮. "𝗞𝗮𝗱𝗮 𝗸𝘂 𝘄𝘂𝗰𝗲 𝗯𝗮𝗸𝗮 𝘀𝗵𝗶𝗴𝗮 𝘄𝗮𝗷𝗲𝗻 𝗺𝗮𝗿𝗶𝘆𝗮 𝗯𝗮" 𝗔𝗻𝗻𝗶 𝘁𝗮 𝗳𝗮𝗱𝗮 𝘀𝗮𝗻𝗱𝗮 𝘀𝘂𝗸𝗮 𝗺𝗶𝗾𝗲 𝘆𝗮𝗻𝗮 𝗺𝘂𝘀𝘂 𝘀𝗮𝗹𝗹𝗮𝗺𝗮𝗿 𝘀𝗮𝗶 𝗱𝗮 𝘀𝗮𝗳𝗲,𝗾𝗮𝘀𝗮 𝗾𝗮𝘀𝗮 𝘆𝗮𝗻𝗮 𝗷𝗶𝗳𝗮𝗻 𝗳𝗮𝗿𝗼𝘂𝗾 𝗱𝗮 𝗵𝗮𝗿𝗮𝗿𝗮. 𝗝𝗶 𝘆𝗮𝗸𝗲 𝗸𝗮𝗺𝗮𝗻 𝘆𝗮 𝗷𝗮𝘄𝗼𝘀𝗵𝗶 𝘆𝗮 𝗺𝗮𝘀𝗴𝗲𝘀𝗵𝗶 𝗱𝗮 𝗸𝘆𝗮𝘂,𝗱𝘂𝗸 𝗻𝗮 𝗺𝗲𝘆𝗲 𝘇𝗮𝗶 𝘀𝗮𝗸𝗮 𝗺𝗮𝘀𝗮 𝗶𝘆𝗮𝘆𝗲 𝘇𝗮𝗺𝗮𝗻 𝗱𝗼𝗴𝗼𝗻 𝗷𝗮𝘄𝗮𝗯𝗶𝗻 𝗱𝗮 𝘀𝗮𝗺 𝘀𝗵𝗶 𝗯𝗮𝗶𝗱𝗮 𝗮𝗹𝗮𝗾𝗮 𝗱𝗮𝘀𝗵𝗶?. Duniyata na kudi ne 08187255862 𝐃 𝐔 𝐍 𝐈 𝐘 𝐀 𝐓 𝐀 ̶B̶O̶O̶K ̶2 ⱧɄ₲Ʉ₥₳ 𝙋𝘼𝙂𝙀 12 Page 12 Har qasan ranta takejin wata izza tana mamayarta sanda take takowa inda yake zaune yana jiran fitowarta. Kansa a qasa,baima dagashi ba ballantana ya qarewa ginin daya zuba kudi da kudinsa akayi kallo. Burinsa daya yayi ya fita ya wuce inda zaije ya kwanta ya huta,don ya gaji matuqa......ga bikin bude company nan da kwana uku a gabansa,gobe da jibi dinma ya tabbatar baida hutu saboda baqinsa zasu fara sauka kuma. Har bayason kallon komai na gidan,yana tuna masa yadda ta dinga uzzurawa kowa da kalar a siya kaza a saka mata kaza,bayan komai a rubuce yake a hannun kamfanin da ya bawa kwangilar ginin. "Zaku wuce kenan?" Ta tambayeshi bayan sun gaisa ba tare data damu ta tambayeshi komai ba. Kansa ya gyada a hankali,ta gyara zamanta tana kiran sunansa kai tsaye "Muhammad.....inaso ka bani hankalinka da kyau,magana zan maka me muhimmancin da itace ta biyu a rayuwarka da zan sakeyi maka ita". Baice komai ba bai kuma motsa ba,illa dai kawai ya tattara kunnuwansa yana jiran DA WANNE ZATA ZO?. "ka san wa na aura maka?.....zabin raina" Ta masa tambaya da amsa gaba daya. Yanayin datayi maganar ya sakashi daga fararen idanunsa masu tarin kwarjini ya dan kalleta,akaci sa'a itama shi take kallo,sai ta jinjina masa kai "Eh......itadin zabi na ce,saba mata wulaqantata ko tozartata tamkar ni mahaifiyarka mariya ka yiwa hakan.......ina me baka umarni ka riqeta kayi mu'amala da ita kamar yadda kowanne namiji yake mu'amala da matarsa da yakeso.......zan iya komai akan cusguna mata muddin kayi......idan nace komai kuwa ciki harda fushi dakai me tsanani". Bai shirya ba a wannan karon ya daga kansa da sauri ya sake kallonta "Wacece ita?......meye shirinta?.......dame ta shigo?" Sune tambayoyin da har a cikin mota yakai maimaitawa cikin ransa. Cikin kowanne jijiya dake kai jini zuwa zuciyarsa cike yake qyamar yarinyar da qaqqarfan zargi a kanta,baya shinshino alkhairi ko qwaya daya a kanta,ta kowacce fuska ITA DIN SHARRI CE. Tun daga ranar daya fahimta itace zabin maamah data fara saukar masa da zazzafan umarni da maganganu a kanta.....tun daga ranar daya fahimci ita dince dai wannan wadda tayi fashin online wa kamfaninsa kudaden da ko namiji me taurararriyar zuciya da tsananin taurin kai iyakarsa kenan......tun a wancan ranar ya sake tabbatarwa kansa akwai wasu abubuwan ma masu yawa da bai sani ba a kanta.....amma koma meye.....koma mene zai tabbatar ya koya mata darasin rayuwa.......zai sauya mata DUNIYARTA da kalar horon da ba zata sake gigin aikata irin rayuwarta ta baya ba......zai sakata tasan meye ainihin TARBIYYA GIRMAMAWA KUNYA DA GASKIYA. Tsaiwar motarsu shine abinda ya fincikoshi daga duniyar tunani zuwa ta zahiri. Ya waiwaya yadan dubi farouq dake qoqarin baiwa guard din da sukazo dasu umarnin yadda shigarsu zata kasance. Ko sau daya farouq bai katse masa tunanin ba ko ya sako masa hira. Wani irin mutum ne daya karanceshi ya kuma fahimceshi sosai,yasan babu yadda zai shiga wajen mahaifiyarsa bai fito da guzurin damuwa ba,shiga lafiya da fita lafiya duka tamkar sa'a ce a wajensu,wannan ya sanya bai fiya masa katsalandan akan kowanne yanayi yaga ya fito dashi ba. A nutse ya dinga bin tsarin ginin da kallo. Baisan inda farouq ya samo gidan ba,don basa cikin gidajensa sam sam,saidai kuma ya cika da mamakin yadda tun daga farfajiyar gidan ta zama sak irin yanayin ginin da yake so,kuma zabinsa. "Alhamdulillah" Farouq ya furta yana dubansa,shima shi din ya kalla,yaja numfashi kadan sannan yace "Shikenan?,hankalinka ya kwanta?,saika wuce gida ka kwanta" Murmushi kadan farouq ya saki,ya miqa hannu bayansu. Kyakkyawan bamboo basket ya fiddo,wanda aka yiwa wani irin ado da tsari,can qasan ransa yana jin tsoro sosai kan yadda yake ganin rashin baiwa komai daya shafi auren muhimmanci daga wajen fu'ad din. Baya jin tsoro akan zaiyi wani maras kyau ba......saidai bashi da tabbaci ko guarantee din zaiyi komai daidai. "Ga tsarabar amarya" Ya fada yana ajiye basket din a tsakaninsu. Harara ya watsawa farouq din sannan ya fara yunqurin bude murfin motar,sai daya fice din sannan yace masa "An gaya maka harda ni a wannan wasan yaran?" "Please mana fu'ad,waye ya gaya maka ana shiga wajen amarya haka?,take it.......it's sunnah fa" Baiko waiwayeshi ba ya fara nufar hanyar dake nuni da shine ainihin qofar shiga gidan gaba daya. "Aurenma sunna ne kuma jihadi zanyi". "Jihadin daukan fansa?" Ya fada a ransa a fili yana dariya qasa qasa. Murfin motar ya balle shima ya biyo bayansa duk da baida niyyar shiga cikin gidan don duka ba tsarinsu bane,a qasan ransa yana fata da addu'ar Allah yasa reshe ya juye da mujiya. Dab da bakin kyakkyawar qofar ya dukansu suka tsaya kamar wadanda aka yiwa umarni,a nutse farouq ya sunkuya ya ajiye basket din sannan ya dago yana duban tsakiyar idanun fu'ad. Koda baiyi magana ba fu'ad din ya fahimci magana yake gaya masa da idon. Farouq ya cancanci kowacce girmamawa da qauna,don haka sai ya sunkuya kawai ya dauki basket din yaci gaba da takawa "Muhammad" Yau farouq din ya kirashi da zallar sunansa da ya jima da manta rabon da yaji ya kirashi dashi. Waiwayowa yayi suka hada idanu. "Don Allah......kayi dukkan abinda ya dace,ka riqeta yadda ake riqe kowacce macen aure". Idanu fu'ad ya lumshe yana budesu lokaci guda,shima nasa idanun cikin na farouq "Banyi maka alqawarin zaman aure irin na kowanne miji da mata ba......ban maka alqawarin cewa zataji dadi kaman kowacce mace ba.......amma zan kyautata idan ta kyautata.......manufar aurendai kuma banajin zata canza,dole tayi wannan karatun,saidai shima zaizo a duk yanayin data zabi yazo" Daga haka ya juya yana shigewa don bayason farouq ya sake neman karyashi da kowacce kalma daga bakinsa. Ba zata iya cewa ga yanayin data wanzu a ciki ba tunda su momma bahijja da sauran mutanen da basufi ashirin ba suka juya suka barta a gidan da suke fama jaddada kyau da tsaruwa da kuma dukiyar dake ciki wanda babu daya a ciki da yayi mata. Ko bayan wucewarsun shuru ne yaci gaba da wanzuwa cikin gidan,jifa jifa tana jin tamkar haushin kare daga dan nesa kadan daga inda take. Ko sau daya bata janye mayafin kanta ba,saima qara duqunquna da tayi tana daga zaunen saboda yadda azababben zazzabi yake sake sauko mata. Wani irin tsoro mara misali yana saukar mata,kalar tsoron da bata taba jin irinsa ba. Empty takejin kwanyarta,kaman an kwashe komai dake ciki an zuba tsoro da rashin nutsuwa,sai muryar matar dake da sunan surukarta a yanzu wadda keta mata kai kawo ita da dukkan dokokinta cikin tsakiyar kanta tamkar ana mata bita kada ta mance. "Assalamu alaikum warahmatullah" Ya furta qasa qasa yadda baya zaton akwai wanda zai jishi,saidai don kawai yasan sallamar wajibi ce a musulunci koda babu kowa cikin gida,Ko ina da haske tarwai tamkar rana,ba wani qwai da yake a kashe. Da idanu yake bin parlor din da kallo,wani tsari me kyau da ya dace da ra'ayinsa tamkar dashi farouq yayi shawara wajen tsarin gidan,tun daga kan color na paint dana furniture din. A nutse yaci gaba da takawa cikin parlor din hannunsa zube a aljihun shaddarsa. Bai tsaya ba sai daya isa tsakiyar parlor din,ya aza basket din hannunsa saman wani dan qaramin table dake tsakiyar falon. Juyawa yayi yana ci gaba da bin kowanne makunnin fitila dake falon yana kasheshi daya bayan daya,har sai da hasken daya rage kawai dake farfajiyar gidan wanda ke ratsowa ta lafiyayyun curtains din da aka zagaye falon dashi. Sai daya tabbatar ba wani sauran abinda ya rage sannan ya sauya akalarsa zuwa upstairs da yake kyautatan zaton a can ne sashensa yake. Stairs na farko kadai ya taka wayarsa tayi qara. Ya dakata ya sanya hannunsa a aljihunsa yana cirota da niyyar kasheta gaba daya,don a matuqar gajiye yake,baya buqatar duk wani abu da zaiyi disturbing nasa. Sanda ya bude da nufin kashewar saqo ya cika screen na wayarsa. *_welcome home mr jadda,Its strongly warning Cease all preparation,Stop all activities,good night,have a nice night_*. Maimaita karanta saqon yayi kusan sau uku,zuwa yanzu ranshi ya fara baci,ya kuma hango zallar rainin wayo daya fara shiga cikin lamarin. Koma su waye suna bibiye da duk wani motsi nasa kenan?. A irin wannan saqon da suke aike mishi,ya tabbatar inda suna da ikon cimmasa da tuni sun cimmasa din. Da baya ya dawo ya zauna saman daya daga cikin kujerun falon wadda tafi kusa da stairs dinsa. Mutum uku ya nema,ya aike musu da komai,sannan ya saka binciken cikin schedule dinsa na gobe,ya kashe wayar ya jefa a aljihu ya miqe a nutse yana wucewa saman. Babban parlor ne da akayi masa wani tsari na musamman,wanda ke dauke da dining area well designed,sai dakuna bedroom biyu da Master room guda daya dake da lafiyayyen balcony da zai baka daman ganin gidan gaba daya gaba da baya. Abinda ya bashi mamaki komai nasa an jera masa,kayanshi da komai nasa,abinda farouq kadai bai taba ba abinda ya shafi dakin sirrinsa dake wancan gidan nasu. Master bedroom din ya zaba,ya tura ya shiga yana rage hasken fitilun,ya qarasa a hankali ya zauna daga bakin sofa bed ya ware hannayensa dake saman cinyarsa yana karanto addu'o'in wanzuwa cikin sabon muhalli *_DUNIYATA LITTAFIN KUDI NE_* 08187255862 𝐃 𝐔 𝐍 𝐈 𝐘 𝐀 𝐓 𝐀 _zafafabiyar_ ̶B̶O̶O̶K ̶2 ⱧɄ₲Ʉ₥₳ 𝙋𝘼𝙂𝙀 13 Page 13 yana sauke dubansa akan ko ina. Bai jima ba ya shafa duka addu'o'in sannan ya miqe. Har cikin ransa yana jin gidan yayi masa,komai ma na gidan kuma ya dace da tsarinsa,tabbas farouq din dan uwa ne kuma amini ne na gaske. Bathroom ya shige kai tsaye,ya hada ruwa me dan dumi kadan bame yawa ba,don garin an dan fara zafin da ake sanya rai zai kaimu zuwa ga damuna. Sosai yayi wanka,ruwan dumin ya ratsashi,ya hada da alwala ya fito. Wasu milk color pajamas ya sanya masu tsananin taushi na kamfanin Ralph Lauren,gray color da suka fidda haskensa da kuma wani kwantaccen kyau nasa daya mallaka,idanunsa sunyi laushi sosai saboda tsananin gajiya,don a daddafe yayi wuturi kadai ya wuce saman gadon. Sasai yaja numfashi yana furzarwa sanda gabbansa suka samu sakewa sosai cikin tattausan gadon da aka lullube da luxury bedsheet dan qasar italy kamfanin feretti. Sosai yaja qamshin da yakeyi har can cikin cikinsa sannan ya fesar da iskar waje. Qamshi......qamshi yana daya daga cikin abinda ke matuqar burgeshi a rayuwa,shi yasa yawa yawan gift din da yake samu suna da alaqa da abu me qamshi,walau turare body mist ko makamancin hakan......farouq ya dade da sanin wannan,shi ya sanya ya saka company din da sukayi aikin shirya gidan suka tsumashi da qamshi. "Ko zata iya tsaftace gidan ya zauna a haka?" Ya raya a ranshi,sai ya tabe baki yana juyawa zuwa barin hannunsa na dama gami da jan qaramin tsaki. "Ruwanta tayi tsafta ruwanta kada tayi" Ya raya a ranshi. Abu daya ya sani shi din zamansa a gidan bame tsaho bane,don zuwa yanzu dole ya fara tabbatar da tsaiwar company dinsa na abuja da za'a bude kafin ya sakar musu. Wani abu kadan yaji ya taba ransa daya tuna yawan massages da yake samu na barazana akan company din "Hasbunallahu wa ni'imal wakeel" Ya furta murya qasa qasa (Shin kinsan qarfinta kuwa?,kisan aikin da take yiwa me yawan ambatonta?,damuwa gareki?,ciwo ne?,ka maqiya suka sakaki a gaba?,ki kamata qamqam ki hada da salatin annabi kisha kallo,Allah ya bamu dacewa yayi mana maganin damuwoyinmu ameen). *******Ba zata ca ga sanda wahalallen baccin dake cike da mugun zazzabi ya dauketa ba,ita dai ta bude idanunta ne kawai ta ganta kwance daga bakin gadon,wanda ta tabbatar da tayi mugun juyi cikin baccinta ba abinda zai hanata fadowa. Tsoro gaba daya ba dabi'arta bane,amma kuma tun a jiya ta fuskanci yana neman samun wajen zama cikin zuciyarta da ruhinta. Tsoron abu guda kawai zata iya cewa ta fahimta.....girman gidan data tabbatar yafi qarfin zaman mata hudu ma da iyalinsu.....alamun motsi da shigowar motarsu dama fitar da motar ta sakeyi,daga haka bata sake jin komai ba amma kuma tsoron bai saketa ba. Idanunta ta maida ta lumshe. Ba ciwon kan zuwa yanzu,ba kuma zazzabin,saidai tana fatan rufe idanunta da tayi dinnan ta budesu ta samu komai ya koma mafarki......komai ya shafe tamkar bai faru ba. Saidai inaaa.....akace qaddara ta rigayi fata,koda ta bude komai yana nan kamar yadda yake,agogo naci gaba da tafiya ba tare daya koma baya ko na second guda ba,wannan shi ya bata tabbacin babu abinda zai canza din,don haka ta yunqura ta miqe da wata irin kasala tana sauka daga saman gadon. Qofa guda daya da tafi kama data bandaki ta nufa. A hankali ta shiga kamar me tsoron wani abu kada ya kamata idanunta nabin kowanne sashe na bandakin da kallo. Komai luxury ne kuma designer daya sanyashi yasha banban da toilets da dama. Sai data bata lokaci tana qoqarin tantance komai,sannan ta isa sashen wanka dake dauke da jacuzzi da bathtub,ta soma zare kayan jikinta. Ko ina na jikinta ya mata nauyi,sam ba dadi saboda nuqurqusar zazzabi,uwa uba kuma akwai rashin sabo na kwanciya ba tare da tayi wanka ba,don haka yanzun kai tsaye taji wankan tafi buqatar yi kafin komai. Sanda ta isa ga closet dinta kuwa sai taji gaba daya ta raina duniyarta ta baya,duk yadda taso abun kada ya burgeta amma hakan bai samu ba,dolen dole ma ya burgeta,komai a jere a tsare tamkar wani hamshaqin boutique daya amsa sunansa ta fannin saida komai da komai. Sai yanzu ta fahimci maganar da hadiyya takeyi bayan sun dawo daga gidanta,suturu ne da batasan iya sanda zata kammala sakesu ba,kusan komai ya cakude,kayanta na gida da wadanda ta taras a nan,bata ma iya ganin natan kwata kwata,duk yawa ta suturarta kuwa sun boye tsaf cikin closet din. Batason ta wahalar da kanta da yawa don bata da wannan energy din,dole ta zabi atamfa kawai riga 3quater da straight skirt ta saka. *******Tun daga daren jiya data dawo daga gidan maamah din wato mariya,bata samu wani cikakken lokaci daya haura mintuna talatin ba cikin tunani ba. Kowanne motsi da zatayi yana motsa mata da tsananin kwadayin cikar burinta,wato wanzuwar jininta cikin jinin mamallakin kamfanin sarrafa gold da diamond din. Ta sani......akwai wasu tsauraran hanyoyi daya kamata ace an sharesu fetal kafin takai ga haurawa izuwa nata bigiren......to amma shin.....mallakar fu'ad a hannun mariya kamar yadda takeso zai iya zama mataki kuma mabudin tata nasarar?. Amsoshi guda biyu ne wato eh da kuma a'ah. Eh idan har tayi nata aikin akan hajiya mariya tazo hannunta.....ita din zata zame mata tsani na mallakawa tata shalelen fu'ad. Aah idan har ta gaza samun mariya a hannunta ko kuma fu'ad ya gagara zuwa hannun mariya kamar yadda take buri......shin me zai hana tayi nata aikin itama daga gefe?,tayi amfani da tata basirar?. Wannan tunanin kadai ya sanyata yankar asubahi,bata kuma tsaya a ko ina ba sai a gaban babban bokanta wato BAHAGO. Maida foldable basket din me zip tayi ta rufe gami da zuge zip din,sannan ta maida idanunta kan zuwaira dake zaune a gabanta "Ina fatan kin riqe dukan baya naina......don a haka nakeso su shiga kunnuwanta tamkar ni nake bayanan......bana buqatar mantuwa ballantana ganganci ko kuma kuskure zuwaira.......zaki zauna kuma a iya matsayinki na 'yar aiki kawai" Kai zuwaira ta jinjina mata. Taji dadin wannan matsayin sosai da maamah ta dauka da danqa mata,ta wannan hanyar kawai zata nunawa hajja qarfin mulki da isarta akan maamah din. Saidai kafin tace komai anyi knocking daga waje "Waye ne?" Ta tambaya cikin qosawa,don ta fara gajiya da yawan baqin da suketa zuwa ganin gida. Jiya a daren bata kwana da kowa ba cikin gidan,tun a daren kowanne baqo ta sanya aka dinga dibansu ana kaisu gida,na wani garin tunda asuba aka debi hanya dasu. "Nice......baquwa kikayine tace na gaya niki" "Baquwa kuma?" Ta tambaya a mamakance,don bata tsammanin samun baquncin kowa a wannan lokaci,hasalima ta gayawa malam Sa'adu kada a sake bari kowa ya shigo,koda sun shigo ta barwa masu aiki sallahu ko waye a gaya masa tana hutawa ne. "Wacece baquwar?" Ta tambaya kai tsaye cikin bacin rai "Hajiya harira" Yarinyar ta amsa mata kai tsaye "Shigo da ita" Itama ta bada amsa kanta tsaye,saidai kuma can cikin ranta tana mamakin abinda ya kawota,don a jiya sun rabu ne tanata mata tsiya,ba zata kuma ganinta ba sai ta huta da kyau. "Kada dai ace har kin watstsake hutun kuma ya qare?" Maamah ta fada tana tsokanarta. Wani murmushi ta saki mai nuna alamun akwai damuwa. "Ina naga ta hutu mariya?,matsala ta tasomu gaba tun cikin daren jiya?". Idanu maamah ta fiddo tana matsa mata wajen zama "Subhanallah.....ni wallahi har kin sanya gabana ya fadi......matsala ko yaya take banson jin koda sunanta,me kuma ya faru?". Baki ta tabe tana zama kafin ta bata amsa "Waini harira za'a gwadawa iya shege?.wai qanin mahaifin laila ne yazo yakeson gwadamin qaramin shege ne shi.....lallai lallai wai ya bada laila.....aure nan da wata guda me zuwa". Ido maamah tadan fiddo a mamakance "An gaya masa a ina yanzu ake hakan?,ya akayi kika bari yayi wannan bunqasar hajja?". Kai ta girgiza irin kana cike da tsananin takaicin nan "Ki barni dashi......zan gwada masa tawa iyawar indai harira nake.....shi yasa kika ganni gab da takewar rana.....ajiyar laila nakeson kawo miki". "Laila ai d'iyata ce.....wannan bazai zama matsala ba". "Shege ne fiye da yadda baki zato,shi ya kusan zamemin matsala zamanin zamana da abbansu.......inda zai yiwu kuma ba takura.....kiyimin wannan alfarmar ki ajemin ita gidan fu'ad,don na tabbatar a can dinne ko daga qiyama ubansa zai dawo bai isa ya shiga da sunan koda ganinta ba ballantana daukota......wadannan qedarun sun isheshi". *_DUNIYATA LITTAFIN KUDI NE_* 08187255862 𝐃 𝐔 𝐍 𝐈 𝐘 𝐀 𝐓 𝐀 ̶B̶O̶O̶K ̶2 ⱧɄ₲Ʉ₥₳ 𝙋𝘼𝙂𝙀 14 15 Da farko maganar taso yiwa maamah din banbarakwai,amma koda ta tuna wacece hajja a wajen ta da kuma tata fafutukar da suka gama yi tare suke ma kuma kanyin sai taji wannan din ba komai bane.....ai rama halasci sai dan halak,banda ma plan din da take dashi batajin zai zama wani abun damuwa don laila zata zauna gidan. Ta tabbatar bata da matsala da laila,ko ita din tana iya zama me sanya musu idanu akan plan dinsu. "Kada ki damu hajja,ni ba abinda bakiyimin ba,kinfi qarfin haka a wajena.....hakanma qarin samun tsaro ne,don yau nakeson tura zuwaira ta zauna dasu ta dinga sakamin ido akan komai". Murmushin qasan zuciya hajja ta saki,bahago shu'umi ne fiye da yadda take zato,ya gaya mata,ya sake gaya mata dama ba damar musu......mariya ba zata iya musanta mata ba. "Na gode sosai mariya....Allah ya saka da alkhairi ya qara zumunci". Kai ta girgiza tana murmushi "Ba wannan tsakaninmu,kinfi qarfin komai a wajena......ko yau tana iya shiryawa sai zuwaira ta biyo ta dauketa su wuce,don banason magariba tayi basu isa gidan ba" Ta fada tana daga wayarta ta duba lokaci. So samu ace tun da safen nan ya karya da breakfast din yarinyar da zai zama lullube da makamanta,to amma sannu sannu bata hana zuwa saidai a dade ba'aje ba. Da wani irin farincikin samun nasara ta isa gida. Ta samu laila din zaune a falo tana kallo. Kusan tunda ta kammala karatu aikinta kenan. Hajja tayi tayi a samar mata aiki ta fara tace sammm ita ba zata iya yawo a gari kowacce safiya ba,hasalima ba zata iya barin baccin safe ba,idan ta barshi waye zaiyi mata shi?. Sai data sha ruwa sosai da lemo,sanyinsa ya sanyata ta fara dawowa hayyacinta sannan ta maida dubanta kan laila dake matse matsen waya. "Mansura ta kawomin kayan nan kuwa?" Kai laila ta girgiza alamun a'ah ba tare data dauke idanunta daga kan wayarta ba. Hotunansa ke matuqar jan hankalinta,kullum kwanan duniya ta kalleshi kota tuna dashi sai taji kaman bata tare da nutsuwarta. Tsaki hajja taja ta jawo wayarta tana mita ita daya "Yarinyar nan inajin sai taje gidansu tayi kwana biyu sannan zata shiga hankalinta". Dab da kiran data mata zai shiga sai gata ta shigo. Niqi niqi dauke da kaya wanki a wanke a goge a hannunta. Mansura daya daga cikin surukan hajja da suke rayuwa gida daya,suke kuma karban duk wani mulki isa da izza tata hannu bibbiyu don ba yadda suka iya,an dauresu da duk wani zaren sihiri da zai bata damar mallakarsu kamar yadda ta mallaki mazajensu. Ko sallamarta bata amsa ba sai harara data jefeta dashi "Uban me kika tsaya yi?,na baki wanki tun bayan asuba da kadan amma sai yanzu zaki gama don bakisan muhimmancin kayan ba?" Bata amsa mata ba saboda nauyin kayan har sai data zubesu. "Kiyi haquri hajja,sai dana sallami yara suka wuce makaranta,abbansu ya fita kasuwa sannan....." "Sannu dadi 'ya'ya dadi miji,bakisan aikina gaba yake da nasu aikin ba su duka?,kada ki sakemin irin wannan?" "Kiyi haquri" Ta fada kanta a qasa,saita janye kallonta daga kanta tana sake jan tsaki "Laila tashi ki kwashe kayan nan ki zuban a wardrobe". Sai sannan ta cire kanta ta kalli kayan "Kai.....gaskiya hajja sunyimin nauyi bazan iya ba.....saidai a barsu a nan,zuwa anjima idan na tashi na kwashesu daya bayan daya". Tsaki hajja din ta sake ja ta maida dubanta ga mansura din "Kwashesu kikai min wardrobe,kuma bance ki zauna ba bare ayimin bincike a daki". Itadai batace komai ba ta tsugunna ta kwashe ta wuce dasu. "Zaki ajiye wayar nan muyi magana ko sai na fasata?" Hajja tayi maganar da daga murya,abinda ya sanya laila kashe wayar ta ajiye agefe,sannan ta juyo wajen hajja "Gani" Sai data dire cup din hannunta sannan tace "Kaman yadda nasha gaya miki ina da plan ina da tanadi a kanki.....tanadina ba kowa bane face muhammad fu'ad jadda.....mamallakin jadda diamond chore resources.....dan qawata mariyah" "Ahhhhhh" Laila ta fada tana fidda idanu cikin tsananin mamaki da kuma gigita. Wani abune da bata taba kawoshi cikin kanta ba,hasalima batasan akwai qawance har haka tsakanin momynta da mahaifiyarsa ba "Wasa kikemin hajja?" Ta fada tana kallonta sosai gudun ganin samu da rashi "Na taba wasa irin wannan dake?" Maimakon ta amsa mata saita daka wani irin tsalle tayi kanta ra ruqunqumeta. "Wayyo Allah mamana......i love you so much mamana......you fulfill my dream" "Kinga shashasha zata karyani......da Allah zauna muyi magana dake don gidansu zaki koma da zama na wani dan lokaci" Ido ta sake watsowa waje,tana jin komai kaman cikin shirin film ko labarun hikaya "Serious?" "Ubanki" Ta fada tana watsa mata zagi da yatsu biyar,saita saki dariya ta koma tana zama din kamar yadda hajja ta umarta. Baki ta daga zata watsawa mansura kira sai gata ta fito "Yauwa saiki wuce ki tafi,ki rufen qofa.....ki gayawa madeena nan da minti talatin ta dafamin madara ta kawomin,wallahi kuma aka wuce haka sai ranta yayi mummunar baci". Kai a qasa ta amsa mata ta juya tana ficewa. Sai data fita din sannan ta maido hankalinta ga laila "Kina jina ko?" 𝙎𝙖𝙗𝙧𝙚𝙚𝙣 Sake duban lokaci tayi,sha biyu saura na rana. Tunda ta farka tayi wanka da sallolinta bataji motsin kowa ba,don hatta securityn dake aikin kula da gidan bakajin motsin kowa,sanin da sukayi cewa hayaniya da motsi me qarfi na daya daga cikin abinda boss din nasu bayaso. Uwa uba ma su dake first gate bata yadda na ciki kamarta zai iya jiyosu. Bawai yunwa takeji ba,amma a jikinta takejin ya kamata ta sawa cikinta koda ruwan dumi ne. Kaman ba zata fito din ba amma ta miqe,ta lalubi mayafi ta lullube jikinta sannan ta sanya plate shoe dinta na jiya ta fara nufar qofa ba tare da tasan takan gidan ba ko kuma daga inda zata fara ba. Rufaffen hallway din ta soma ratsawa,wanda aka qawatashi da wani irin wall led light na musamman,da wasu irin qananu masu haske da suka sake fidda ainihin kyan wajen. Tattausan runner carpet ne shimfide duka tsahon wajen tsakanin kowanne qofar daki zuwa na dan uwansa an qawatashi da wasu irin nature frames masu daukan hankali. Daga bangon dake facing naka kuma,babban console mirror ne da zai baka daman ganin kusan dukka jikinka har kusan cinyoyi. Akwai plants masu kyau data gani cikin flower vase masu wani irin daukan hankali,bata sani ba masu kyau ne ko ma decoration. Guri ne daya cika da hasken da koda allurarka idan ta fadi zaka iya tsugunawa ka dauka,ko ina fes da wani irin matsanancin tsaftar da babu qura ballantana ka saka ran samun wani abu waishi datti saman lafiyayyen marbles din dake lullube kuma shimfide a qasan wajen. Duk zuqar iska guda daya idan tayi da qamshi take kai mata har hanjinta,qamshin da sam bata da tabbacin daga ina yake fesowa ya karade kowacce iska dake kai kawo a wajen duk kuwa da a rufe hallway din yake. Idanunta kafe akan staircase din dake gabanta. Batasan ina bane bata kuma fatan sani,nan din inda aka ajiyeta ma kawai tana jin ya isheta harta kammala abinda zatayi tabar cikin rayuwarsu,fatanta daya shine idan ta isa staircase din ta samu wata qofar tsakanin hagu da dama cikin dan lugu biyu da take ganin alamunsa. Ajiyar zuciya ta sauke sanda take dab da bakin stair case din,akwai wasu qofofi hagu da dama,saidai ta daman tafi mata kama da qofar da zata sadaka da wani gurin. Solid wood door ne me qofar biyu data dace da kalan gidan gaba daya dake bata kalan gold and off white,dayan pivot door ne wanda tafi kyautata zaton wani gurin na daban zai sadaka dashi,don haka ta nufi hannun damanta,ta sanya hannu ta murda handle din ta bude qofan a hankali kamar me tsoron wani abu. Wani irin tsararren parlor ne da kana kallonsa zakasan ilimi hankali da dukiya duka sunyi amfani. Well designed parlor me wani irin sassanyan yanayi me jan hankali. Babban swarovski crystal chandelier din dake tsakiyar falon ce kawai a kunne,amma duka fitilun dake zagaye da falon a kashe suke,saidai duk da haka hakan bai hana fitar ainihin kyau da tsaruwar falon da aka qawata da kujerun qasar Italy. Kutsa kai taci gaba dayi cikin falon kamar me tsoron sautin takunta,tako ta ina tsarin gidan yana dada kwance mata kai. Wani irin tsari dake da matuqar sha'awa da daukan hankali. Idanunta suka fada daya sashen falon. Glass door ne da zai baka damar hangen wani guri da aka qawata da wani irin shuke shuke masu launika daban daban masu daukan hankali. Wajen yafi mata kama da qaramin lambun da zai taya mazaunin falon debe kewa. Ta sake wurga idonta.....ba wata qofar a nan data mata kama da qofar kitchen,sai wata qofar shigen qofar farko data bude. Ita ta nufa kai tsaye,tana jin yadda qafafunta suke nutsewa cikin lallausa Italian Versace carpet daya dace ta kowacce fuska da kalar tsarin falon. Steps hudu masu fadi ta soma cin karo dasu,wanda ta nan zata taka ta sauka cikin wani falon na daban da yasha banbam dana farko ta kowacce fuska. Furniture din ciki girma da tsari,saidai kusan komai nacan akwaishi anan,illa na wannan falon yafi na wancan yawa da girma. Rukunin kujeru biyu ya dauka saboda girmansa. Sabanin wancan falon,wannan tafkekiyar tv plasma din da tafi qarfin Wall wooden TV stand din aka girketa samanta ce a kunne. Saudi qur'an ce kunne,saidai kuma sautin karatun sam baya fita. Lullube kowanne bango yake da tsadaddun curtain masu wani irin kwarjini da haiba,kowanne maqale jikin Drapery hardware,abinda zai baka daman ganin qifofin da sukayi saura ta wajen banda yalwataccen dining area da aka yiwa ado na musamman da roman shade curtain da zai baka daman kallon wani sashe na kitchen da glass door ya rabasu. Qaramin tsaki taja tana janye kallonta daga kallon kowanne tsari na parlor din. Finally bayan ta gama duk bulayin ta samo kitchen din da qyar,don haka ta taka a nutse tana hawa steps din da zai sadata da dining din zuwa kitchen din. Sak tayi canma tana kallon kitchen din,don wata aljannar duniyar ce da bata san ta ina zata fara ba. Komai a kitchen din baqonta ne,ba wani abu da zatace ta masa farin sani idan ka debe kayan amfani na yau da kullum da kowanne kitchen ake samu. Ya qawatu sosai da custom cabinets da aka sarrafa da wani irin gogaggen katako datayi imani badai daga qasar nan ba,yabi sauran kayan cikin gidan yazo ne daga wata qasar daban. Tunaninta ya dawo da baya,shin yaushe duka suka samu wannan kudin?,a ina?,da har aka samu daman zuba mata wannan uwar dukiyar cikin gidan?. Anya kuwa bayan mutunci da kawun ya saida mata ba hada harda 'yancin jere ga kowacce diya budurwa ba?. Iya wannan tunanin ya sake sanyawa taji komai na gidan ya fice mata a rai,baya kuma burgeta ballantana taba haskenshi. Taja qafafunta da sukayi mata nauyi tana nufan gas glass stove din tana fatan ta kunnashi daidai kama kowanne. Sai data bata lokaci shi kansa wajen gane kansa sannan ta saki ajiyar zuciya. Taja da baya tana baza ido don hango inda zata samu koda ganyan shayi ne,don dama cimar bata wuce haka. Daga can ta hango wata qofar,ta taka zuwa wajen tana addu'ar Allah yasa ta samu abinda takeso,don duka ta gwada duba cabinets din bata samu komai ba aciki,da alama shi kam banda kayan kitchen din da aka jera ba'a taba komai ba. Cikin sa'a ta tadda yalwataccen guri da yafi mata kama da store saidai na musamnan. Don ba abinda yake zube a qasa hatta kuwa da buhunhuna da kwalaye,kusan duka wajen shima an masa kanta sosai kamar kanti ko shago,an saka komai a bangarensa daidai da kwalayen maggi kuwa. Daga gefe babbar freezer ce wadda batabi ta kanta ba,don ko sha'awar budewa bataji ba,to ta bude taga me?,ba wannan ne a gabanta ba. Bangaran spices na tea ta nufa,ta bude ta debi kowanne daidai yadda zai isheta,daga wannan ba abinda ta qara ta dawo ainihin kitchen din,ta bare tukunya daya,ta nufi sink ta kunna famfo ta debi ruwa,sannan ta dawo ta kunna gas stove din ta dora bayan ta zuba komai. Minti goma tsaf ya tafasa,ta soma duba mazubin da zata juye ta wuce dashi,don sam batason zamanta kitchen din. Tea set ne kala kala,ta rasa ma wanda zata dauka. Taja qaramin tsaki still,komai na gidan ya fiya fi'ili da feleqe,tunda ta tashi komai ma sai tasha wahala take laluboshi,iya yau kawai.....neman kitchen da dafa tea ya zame mata alaqaqai?,ina ga sauran rayuwarta cikin gidan. *_DUNIYATA LITTAFIN KUDI NE_* 08187255862 𝐃 𝐔 𝐍 𝐈 𝐘 𝐀 𝐓 𝐀 _zafafabiyar_ ̶B̶O̶O̶K ̶2 ⱧɄ₲Ʉ₥₳ 𝙋𝘼𝙂𝙀 15 16 Qarshe dai wani Wedgwood tea set din qasar chaina ta dauka ruwan sararin samaniya,ta juye duka ta zuba sugar a mazubin sugar din sannan ta dauka tray na set din cak tana wucewa ciki dashi. A yanzun tafi fahimtar hanyar da take komawa ba kamar dazu ba. Tabbas duk yadda takai gason ta kushe komai ta kasa,duk.yadda takeso komai kada ya burgeta a gidan hakan ya gagara,dole ta sallama saidai still zuciyarta na gaya mata "Allah yasa da kudin halal akayi komai" (😂 yarinya tunda dai kin fara mora ai magana ta qare). Bata tashi tunawa da personal wayan da ta bata ba sai data kusa kammala shan tea din. Qarar wayar ya Haifa mata da wata irin faduwar gaba. Wayace data jaddada mata cewa ta bata ita ne kadai saboda personal use dinta,bata bata ita don ta kira kowa ba sai ita kadai. Hannu ta tura qasan inda wayar ta fada tun a jiya da zazzabi ya kamata,ta duba fuskar wayar sunanta ya bayyana baro baro 𝙈𝙖𝙧𝙞𝙮𝙖 𝙨𝙖𝙡𝙞𝙝𝙪 𝙖𝙙𝙖𝙢 shine sunan data zabi ta sanya mata saman number. A zahiri tana qoqarin hana kanta daga wayar ne,don bata da buqatar jin muryarta kwata kwata.....amma a badini sai taji kamar ana tilastata daga wayar. Can qasan zuciyarta ta dinga jin bata da wani sauran sukuni saina daga wayar,a sanyaye ta latsa ta kuma kara wayartata a kunneta "Amarya.....ina fatan kin tashi lafiya?" Sai da taja wani nannauyan numfashi tana qoqarin daidaita kanta kafin ta furzar da iskar a hankali a kuma sirrance "Ina kwana?" Ta fada da sassanyan murya. Murmushi maamah ta saki,da gaske aikinta na jiya ya ratsata yadda takeso,ta tabbatar banda haka bataga alamun zata samu gaisuwa wajen yarinyar ba koda na minti daya ne "Lafiya lau....ya baqunta?" Batasan wacce kalar amsa zata bata ba,don haka ta zabi tayi shuru. Itama shirunta ba shine damuwarta ba,isar saqonta zuwa ga kunnuwanta shine damuwarta don haka ta dora. "Zuwa anjima kadan zan aike miki da me aiki da kuma 'yar 'yar uwata......zata zauna daku nadan wani lokaci ne.....me aiki zatayi aiki ne kadai da umarninki,da tayaki abinda kike da buqata......amma kula da muhammad da dukkan abinda zaici ban dorawa kowa ba yana wuyanki......kada ki damu da wanzuwarsu.....dukansu sunsan da tafiyar.....saboda haka ba buqatar boye boye wajen gudanar da aikinki,kiyi komai kawai gaba gadi. Abu na gaba muhammad bame sauqi bane.....kada ki sanya rai koki damu da rashin cin abincinki a zangon farko......kawai kici gaba da dafawar.....kici gaba da shiga lamarinsa.....kici gaba kuma da dukka qoqarin ki na ganin yaci yasha din.....yana da tsananin miskilanci......yana kuma da tsantsamin da sai kin zama me tsananin tsafta kafin ki samu abinda kikeso.....ina fata kin fahimta?". Can qasan ranta suya sosai zuciyarta takeyi. Tanajin maganganu na taso mata da ya kamata ta maidawa maamah.....amma sai takejin kamar biyayya wa umarninta ya zame mata tilas ne kawai,ba buqatar musu ballanta jayayya "Kin jini?" Ta sake tambaya don tabbatar da taji komai din "Eh naji" "Yauwa.....saikin sake jina ko?,idan akwai tambaya ko wani abu daya shige miki duhu......qofa a bude take". Kasa cewa komai tayi,sai kawai ta sauke wayar daga kunnenta tana ajeta gefe tare da binta da kallo. Shawarwari kala kala zuciyarta ke bata game da wayar,wata zuciyar na cewa ta zare layin ta karyashi ta yar,wata nace mata ta kashe wayar ta wurgar a dustbin,wata kuma na gaya mata ta sakata a silent tayita kira ba'a dagaba,amma daga qarshe ji tayi ko guda daya ba zata iyayi ba. Bawai don bata buqatar hakan ta faru ba....aah haka kawai taji aikata hakan bazaiyi ba,saita nutsa yatsunta cikin gashinta kawai tanajin kanta kamar ana yamutsashi......umarninta kadai take da muradin cikawa. Kusan saman idanunsa hasken alfijir ya fara keta duhun sararin samaniya yana kore duhun daya mamayeta,duniya ta fara haskaka da siririn hasken nan dake juyewa izuwa hasken rana dake wadatar duniya da halittun cikinta. Wayarsa ya kalla,a gida a lokuta irin wadannan ya kammala duka wasu addu'insa.....yana shiri ne ya fita gym da yake bawa awa daya.....so amma a yau din yadda yakejin jikinsa da sauran gajiya bazai iya komai ba,sai ya miqa hannunsa yana jawo wayarsa da yaga tana haske sanda qarfe bakwai da rabi na safe ya cika. Joshua ne.....ma'aikacinsa dake kula da bangaren marketing da price na gold da Diamond a kamfaninnikansa. Yana cikin manyan ma'aikatan da baya iya tsallakema kiransu. Cike da mamakin kiran sassafe irin wannan ya sanya wayar a kunnensa "Hello......" Fu'ad ya fadi da muryarsa maras hayaniya musamman daya kasance yanzun safiya ce "Hello sir........good morning sir......ina expecting zuwa yanzu baka duba business side news paper da magazines ba ko?" "Morning Joshua.......what's going on?" "Sir......sun karya darajar gold da Diamond duka tsakanin tsakiyar daren jiya zuwa yau da safe". "La'ilaha illlallah" Labbansa suka motsa ya furta a nutse idanunsa suna lumshewa. Daga yadda Joshua ke masa magana adan rude ya tabbatar abun ba qarami bane. "Cool down Joshua......i will be online yanzu in sha Allah" "Okay sir......but sir a irin wannan yanayin da sabon kamfani ke shirin fara aiki akwai hadari sosai a ciki.....akwai barazanar tsayawar abubuwa da yawa mo durqushewarsu......sir inaji a jikina an shirya wannan abunne kawai". "Calm down Joshua,ba abinda zai faru in sha Allah.....let work together okay?". "Okay sir....." Ya amsa da damuwa sosai a cikin muryarsa. Kiran ya yanke yana sauke nannauyar ajiyar zuciya gami da maida hankalinsa kan fuskar wayar tasa. Dole ya miqe a nutse ya fara bincika inda system dinsa suke da sauran kayan aikinsa. Cup rabin qaramin cup tasha taji tea din ya isheta. A nutse ta maidashi ta ajiye tana bin cup din da kallo. Ya mata kyau sosai,amma kuma ba wannan tunanin bane a qasan ranta,ta janye idanunta tana lumshe. Ta ina rayuwa zata fara?,yaya rayuwar zata kasance?. Idanunta ta bude,sai suka sauka akan wayar da matar dake amsa sunan surukarta ta bata jiya. Daga jiya zuwa yau sai takejin komai kamar ya canza. Har a ranta da zuciyarta sam bata jin matar ko kadan.......tana jin wani qaqqarfan abu a kanta da yafi kama da qiyayya......qiyayyar batasan ta mece ba.....saidai koma meye baya rasa nasaba da katsalandan da suka yiwa rayuwarta ita da d'anta. Tanason kiran momma amma batasan me zatace mata ba.....kuma kaman a yanzun ma yayi safiya da yawa ta kirata din. Yadda taji zuciyarta nason karyewa taji bataso......batason ta karaya tun bata gama fuskantar komai ba. Gidan yayi mata shuru da yawa,duk da dama can ita ba ma'abociyar son hayaniya bace....ko a gidansu zaka samu dakinsu a rufe kirif don rage yawan hayaniyar mutanen tsakar gidan nasu,a mafi yawan lokuta ma tafi qaunar shurun,sai takejin wata irin kewa tana shigarta.....kewar huda.....kewar nadra....kewar haneefa. Takan tsinci kanta a wani yanayi maras dadi idan ta tuna dasu.....ta yaya zasuci gaba da rayuwa?. Tana da nutsuwa kadan idan ta tuna suna tare da momma bahijja,tayi imani zata cika abinda tace din,amma duk da haka bata shirya barinsu a wannan matakin ba. Yunqurawa tayi ta miqe dauke da tray din don ta maidashi inda ta daukoshi,tako ina tanaji komai da zatayi amfani dashi a cikin gidan na wucin gadi ne kuma na aro ne a wajenta,bata da hurumin zafafa mu'amala da komai na gidan. A karo na biyu ta sake duban stair case din sanda zata wuce ga qofar da zata sadata da parlor din. Sai a sannan ta sake qare mata kallo sosai. Tamkar gine ginen turawa haka aka tsara gidan,wani irin staircase ne me kyau da aka qawata bangonta da wani irin woods royal frames da shukoki masu kyan launi da fararen furanni qananu qananu. Idanunta ta janye tana jin bata da hurumin maida hankali da wajen,saidai girma gidan yana saka mata shakka da tsoro a ranta,tana kuma cike da shakka da tantamar ita kadai ta kwana ne wai a cikin gidan?. Saidai basket din data gani ajiye saman table din falon bayan ta dawo a kitchen din ya fara alamta mata ba ita daya bace ba. Tana shirin janye idonta ta wuce ciki taji sallama daga parlor din farko. Da dan tsoro da mamaki ta maida idanunta kan pivot door din cikin tantamar wanda yake sallamar. Tsahon second talatin tayi,sai taji ta wuce ciki kawai,don bata jin akwai wani abu a cikin gidan da take da haqqin lallai saita kula da yadda zai tafi,saidai taku uku kacal ta sakejin muryar na sake jaddada sallamar. Sallamar tayi mata nauyin da takeji bai kamata ta wofantar da ita ta Kuma wuce ba,dole ta dawo da baya tana dosar qofar,ta turata ta bude tana saka qafanta kan step din idanunta cikin parlor din. Kamilalliyar macace cikin kyakkywar shiga da lullubi,tana a tsaye,gefanta kuma kyawawan kwanduna ne guda biyu ajiye a gabanta. Murmushin data sakarwa sabreen shi ya sassauto zuciyarta,sannan ya zabge kokwanton dake ciki,saita samu qwarin gwiwar ci gaba da saukowa idanunsu cikin na juna "Ina kwana" Matar data kusan haifarta ta gaidata kafin ita takai ga gaisheta. "Ga waje ki zauna" Tace da ita cikin qarfin hali ba tare data amsa gaisuwan ba. A nutse kuma cikin girmamawa ta zauna,sai itama ta samu gefen kujerar ta zauna tana maida mata gaisuwar "Ina kwana?" "Barka da asuba,mun tashi lafiya?" "Alhamdulillah......ya baqunta?" Ta fada da murmushi da kuma kulawa a muryarta "Alhamdulillah" Ta amsa mata har yanxu tana tunanin wace ita. "Anni ce ta aikoni.....tace kuyi haquri har yanzu akwai baqi cikin gidan,shi yasa ba'a kawo breakfast da wuri ba,amma gashi nan harda lunch don kada ayi delay na kawowan da wuri shi yasa ta hada.... Tace da fatan hakan ba damuwa?" Sunan tadan juya cikin ranta,amma kuma farat daya hankalinta sai yakai kan matar. Murmushi tadan saki tana mamakin damuwar da tayi dasu haka "Ba komai.....ayi mata godiya sosai" Ta fadi tana jin wani abu na daban akan matar. Miqewa matar tayi "Sunana baraka.....dadaddiyar hadimar anni ce ni,zan koma,a huta lafiya" Kai kawai ta gyada mata,har ta fice idanunta suna kanta. Sai ta ajiye ajiyar zuciya tana maido kallonta ga basket din gabanta. Tadan xuba masa idanu tana nazarin matar,komai nata cikin dattako.....kuma komai nata akwai alamun nutsuwa me yawa a tattare dashi,waishin WACECE UWA a cikinsu?,wacce mahaifiyar ta ainihi?. Wannan tambayar kusan ita daya ce abar data damu da ita cikin lamarin kaf,sai ta miqe a nutse kaman zata bar wajen,sai kuma ta fasa,ta tsugunna ta dauki basket din,ta taka a hankali zuwa dining area din da aka qawata da wani dunqulalle kuma mulmulallen dining data kasa tantance glass ne ko kuwa dutse?,ta dora basket din kawai akai,sannna ta juya tana sauka ta wuce zuwa dakinta. Sai daya daidaita komai sannan ya hada connection din duk da yakeso. Bincike ya fara yi a kasuwannin hannun jari na gold da Diamond.......da gaske an masa wani irin mummunar faduwa da bai taba ganin yayi hakan ba tsahon fara kasuwancinsa. Baya ya koma ya jinginar da bayansa jikin kujera yana shafa lips dinsa da yatsansa guda daya. Da gaske akwai faduwa da hasara me yawa data samesu,musamman a irin wannan lokacin da kwanaki kadan suka rage kamfani ya fara aiki. Zai zamana kome xasu fitar ko su samar asara ce a garesu,dole su saidashi a qasa da farashin da aka tsara za'a fiddashi. Saqonnin da aka yita turo masa suka dawo masa akai,ya lumshe idonsa ya kuma budesu yana kiran sunan Allah,sai ya sake maida hannunsa kan system din. Kusan duk wani ma'aikaci dake aiki qarqashinsa na kusa dana nesa sai daya nemeshi. Ya bata lokaci sosai yana urgent meeting dasu,wanda hakan ya daukeshi aqalla a wanni masu dan dama. Baisan kuma ya jima din a zaune ba sai da cikinsa ya fara qara. System din ya rufe yana furzar da iska daga bakinsa. Ya tabbata babu abinda zasu iya sakeyi......dole su rungumi dukka hasarar data tunkarosu lokaci guda...... Akwai manufa.......kuma anyi ne da gayya,kuma hakan ya sake bashi tabbacin dukkanin saqonnin da aka aike masa da gaske suke.....sun shirya shiga yaqin tare dashi.....sun shirya jan daga shi dasu. Sai ya saki wani qaramin murmushi. Sunyi gangancin fara tsiro irin wannan abun dashi......ya tabbatar basu gama sanin ainihin waye muhammad a kasuwancinsa ba.......wannan abun koma waninsa bazai sauyashi ba......bazai kuma sakashi ya tsaida kowacce harka tashi ba. Har a jikinsa yakejin a baqon guri yake,banda haka zuwa yanzu da tuni Ameh ya dameshi da batun abinci. Hannunsa ya miqa ya dauki wayarsa ya kunnata daga kashetan da yayi "Subhanallah" Ya furta da hanzari ganin har azahar ta sanyo jiki. Bai kira anni ba.....bai kira farouq ba,baima kira kowa ba wanda aqalla ya dace ya yiwa kowa bangajiya koda kuwa ba shine ya gayyatosun ba,amma aqalla sabodashi suka zo. Anni ya fara kira amma sai yaji wayar a kashe,yasan har yanzu gidan akwai sauran baqi don haka yafi kyautata zaton uzurin daya sakata kashe wayar kenan. Yayi zaton zai samu saqon farouq amma sai ba tarar ba. Ya danji ba dadi,don haka kai tsaye ya fara kiransa. Bugu daya ya daga kamar dai dama wayar tana hannunsa yana jiran kiran nasa ne. A nutse ya masa sallama,daga can background yana dan jin muryar mutane. "Kaji muryar ango......so fresh" Farouq din ya fada kansa tsaye. *_DUNIYATA LITTAFIN KUDI NE_* 08187255862 𝐃 𝐔 𝐍 𝐈 𝐘 𝐀 𝐓 𝐀 _zafafabiyar_ ̶B̶O̶O̶K ̶2 ⱧɄ₲Ʉ₥₳ 𝙋𝘼𝙂𝙀 16 "Sai yanzu aka tashi kenan?" Farouq din ya sake fada ba tare daya damu da abinda zaice da farko ba a lallai sai ya tsokalo shi "Eh.....ka nemeni ne?" "Wa?,ni?,ya za'a yi na batawa kaina lokacin nemanka?,waya gaya maka ana kiran ango a irin wannan time din?" "To hell with you farouq a'ahhhhh" Ya fada sounding bored kadan kadan. Murmushi me kama da dariya ya saki wanda har sautinsa ya bayyana sosai. "An maka uziri kome zaka fada you're forgiven" Hannunsa ya dora saman sumarsa yana shafawa,ya fuskanci farouq so yake kawai ya haukatashi "Where's anni?" "Na barta a gida tana preparing na walima....." "Ya salam" Fuad ya fada yana lumshe idonsa. Sam ya mance da batun walimar kwata kwata. "Su haajj na yiwa rakiya airport......they're leaving". "My regards to them please.....idan na sake nutsuwa zuwa anjima in sha Allah i will give them a call" "Ance maka daga yau har wani satin an maka uzuri fa.......ka samu nutsuwa yadda ya dace dudu" Ya rigashi katse wayar wannan ya hana fuad gaya masa abinda yayi niyyar fada din,sai kawai ya zame wayar daga kunnensa,qasan ransa yana fassara maganar farouq da kuma sakata a inda farouq din ke nufi "God forbid" Ya fada qasa qasa. Hasashen gaba days banbarakwai yayi masa sanda ya dora tunanin a muhallin da farouq ke nufi,tattara tunanin yayi ya azashi a mizanin shirme gaba daya,ya fara lalubar number amna. Sai data kusa yankewa sannan ta daga "Hamma" Ta fada a shagwabe. "Hamma ka manta dani.....adda tayi taking dinka away.....as far as yadda zata iya" Ta qarasa fadi da qaramar dariya a muryarta da ba sosai ta bayyana ba "You amna.....lovey dovey will never be forgotten........hayaniya yayi yawa amna.......bansan haka ake abun ba" "Hamma yafi haka fa.....don kaqi bada hadin kai ayi komai" Hannunsa ya dora a goshinsa yana furzar da qaramar iska. Shikam ko zancan bayaso,abinda yake gabansa kawai yanzun shine damuwarsa. "Ya gidan?" Ya tambayeta. "Full with 'yan biki dake jiran walimar anni......ina yini hamma" Ta hade amsa tambayar tasa da gaisuwa. "Alhamdulillah.....how about anni da abba?" "Abba dai ya fita tun dazun.....kuma ina jin sai dare zai dawo........anni tana daga baya da mutane" "Okay.....bata wayar" "Okay hamma" Ta amsa shi tana miqewa gami da ficewa. Bai yanke kiran ba saita maida kunnenta,tana tafiya wajen annin tana ta bashi labarai kala kala. Bai yanketa ba yayi shuru yana saurarenta. Yasan halin amna sarai,bata gajiya sam sam da hira. "Kice ameh ya kirani....." "Okay hamma.....ga anni" Saita miqawa anni wayar,ta samu plastic chair daya daga cikin kujerun dake wajen ta zauna tana kallon yadda aka qawata wajen walimar da wani irin tsari me kyau,tamkar wani hamshaqin event center. "Barka da warhaka anni......ya hidima ya rana?" Murmushi ta sauke,har cikin ranta farinciki yana mamayarta idan ta tuna a yau muhammad dinta ya zama cikakken magidanci "Barka kade me babban suna.....mun tashi lafiya zance ko mun yammata lafiya?". Tambayar tata tadan sakashi yaji nauyi,kada itama fa ta dauka wani abune ya boyeshi,kada ta fassara wani abu na daban akan yarinyar ma da bai samu daman ganinta ba "Lafiya anni alhamdulillah" "Haka akeson ji.....na aika baraka takai muku breakfast da lunch.......nayita so nace idan ta isa ta hadani da d'iyata mu gaisa saina sha'afa......in tana kusa bani ita" Rasa abinda zaice yayi,yadan diririce kadan har hakan yaso ya nun alamu a muryarsa,yayin da annin ta dauka wani abunne na daban ya kawo hakan,kodai baiso aji muryarta a fahimci wani abu,don haka ta katseshi "Kaga rabu da ita.....anjima idan kun iso wajen walima ma gaisa.....za'a fara immediately after asr prayer" "Allah ya kaimu anni.....Allah ya qara girma da lafiya" "Ameen ya hayyu ya qayyumu" Ta fada tana jin dadin yadda sam baya gajiya da mata addu'a. Ita ta fara katse wayar,sai shima ya sauke yana kallon fuskar wayar. Inda anni ta sani data qyale walimar nan,duk da ita walima duk inda take albarka ce. Agogo ya kalla har daya na rana yayi,sai ya aje wayar yana jin zuwa yanzu ya kamata ya laluba kitchen ya samu koda tea ne ya sanyawa cikinsa. Duka wani abu daya saba sha da safe irinsu goji berries water da turmeric tea,cinnamon tea da sauransu,wannan ya sanya yake da wani irin cikakkiyar lafiya da kuzarin da idan ya shiga cikin maza kuzarinsa yake fita daban,kaman yadda yake da cikakkiyar lafiya irin ta d'a namiji,wanda yayi imanin banda busy da business daya saka a gabansa suka fatali da komai da yakeji......tabbas da bai isa yakai har wannan lokacin haka ba,dalilin da yasa ya janyewa amfani da wasu abubuwan irinsu ginseng tea,sai time to time idan yana da buqatar hakan,ko ya kwana biyu bai sha ba. Fararen loopers slipper ya sakawa qafafunshi,wadanda suke mahadi ne na fararen pyjamas din jikinsa da suka fidda siga da surarsa. Yanayin fatarsa kadai ya isa ya fadi maka irin wadata da nutsuwa da yake ciki,skin dinsa so fresh da ba lallai ta wata macen ta samu irin wannan kyan da glowing din ba. Sai daya shiga toilet ya daura alwala,ya dauki qaramin towel ya tsane ruwan jikinsa sannan ya maida takalmin ya nufi qofa yana gyara hannun pyjamas dinsa daya tattare. A nutse ta idar da sallara azahar tana maida idanunta wajen sujjadarta. Tana jin idanun a jikinta sunyi mata nauyi,nauyin da bata raba dayan biyu yunwa ce da kuma bacci. Baccin kam tana da tsananin buqatarsa,ita kanta ta sani,saboda ita kanta tasan cewa taci bashin baccin yadda ya kamata,abincinne bata jin akwai muhallin da zata sakashi a cikinta,saidai jikinta na sake gaya mata ya zama dole ta nemeshi. Dole ce ta sanyata miqewa,a nutse ta nade abun sallar,ta gyara yafen dan madaidaicin hijab din data dauko daga closet din nata ta daure igiyar sannan ta juya tana lalubar qofa bayan shawarar da zuciyarta ta bata nata duba cikin kayan da aka kawo ko zata samu abinda zata saka a cikinta. A nutse ya sauko daga saman yana sake jin nutsuwa da gidan da tsarin gidan. Ya dauke idanunsa daga hallway din da yake kyautata zaton shiyyarta ne. Qofan dake damansa ya karya zai bude sai kuma ya fasa,ya koma ya kama handle din wooden door din ya bude yana isa ga falon. Ko ina da komai yana nan kamar yadda ya barshi a jiya,da alamu ba'ayi amfani da parlor din ba kwata kwata. Zarcewa yayi parlor din farko wanda keda kitchen din,ya sauka daga kan step din a nutse sannan ya zarce zuwa dining da hake hango basket akai,da alama saqon da anni tace ta aiko ne. Yana daga tsaye ya miqa hannu a mamakance ya jawo basket din,yadda aka kawoshi haka aka ajiyeshi,da alama ba'a ko budeshi ba ballantana a taba komai a ciki. Waye to ya karba saqon ya shigo dashi?. Ba kowa sai ita wannan shine amsar daya bawa kansa,don ya sani ba wanda zaiyi gigin shigowa cikin gidan saboda sunsan doka da kuma tsarinsa. Duk wani ma'aikaci dake aiki a qarqashinsa,daga cikin company har zuwa cikin gida kowa yana tsayawa iya limit dinsa ne,ba wanda yake wuce qa'idar aikinsa ko kuma limit dinsa. Komai anni ta zuba na duka irin abinda tasan yafiso yaci da safe ya kuma ci da rana,ya sauke qaramar ajiyar zuciya yana sake jin qaunar matar da martabarta suna hauhawa a zuciyarsa. Baiga wani abu da zai taba annin ya bari ba ko wayeshi,take sai yaji ransa yadan baci,ganin kamar ta wofantar da kayan da aka kawo din. Daidai abinda cikinsa yake buqata ya zuba,kafin ya gama duka ya bata wajen saboda rashin sabo,ya manta when last yayi serving kanshi,duk wani motsinsa akwai masi hidimta masa. Tsaki kadan yaja ganin bacin da wajen yayi,ya soma wassafa yadda zai aje masu masa hidima cikin gidan kaman yadda ya saba,don bayajin zai bari ya takura har haka,ya dauko komai cikin qaramin serving tray ya dawo ainihin parlor din,sai ya azashi saman side table. Har zai zauna sai ya fasa,ya dauko remote yana lalubar channel din dake haska rate na dollar pounds da rate na diamond da sauran harkokin kasuwanci. Har yanzu yana cike da mamakin yadda abun ya kasance,duk da iya bincikensa har yanzu ba wanda yasan daga ina faduwar gold din haka rugu rugu ya samo asali. Ya soma sipping pomegranate juice kenan idanunshi suka sauka akan basket din. Tun basket din jiya da farouq ya hadoshi dashi,wanda shi kansa baisan anihin meye da meye a ciki ba. Bacin ran da yaketa qoqarin boyeshi dole a wannan karon ya bayyana kanshi. "What's all these nonsense?" Ya fada can qasa labbansa suna motsawa. Kamar jira akeyi yayi tambayar yaji alamun motsin mutum. Fararen idanunshi ya daga still cup din yana saitin bakinsa,baikai bakinsa ba bai kuma dire ba,ya zube manyan idanunshi a kanta. Karon farko da ya fara mata kallon kai tsaye a rayuwarsa,karon farko da yayi mata kallon da zai iya gane face dinta.....don kuwa a baya zai wahala ya iya cireta cikin mata goma ko biyar idan aka zube masa su. Kwata kwata bata lura da mutum ba sanda take sauka daga steps din zuwa qasa don nufar kitchen,amma da yake cikin dabi'arta akwai sanya idanu da kula da motsin komai da komai dake kewaye da ita,da kuma sanya hankalinta bisa yanayin kowanne abu saita dinga ji a jikinta kamar akwai wani baqon abu da babu shi dazu a parlor din. Juyi biyu ana uku idanunta suka sauka akan nasa........itama karon farko kuma lokaci na farko a rayuwarta datayi masa duba nakai tsaye.....duban dake rataye da abubuwa masu yawan da suka faru. Wani nannauyan abu taji yana fita daga idanunshi zuwa nata yana neman kwarjanta mata shi da wani irin madaukakin kwarjini da bata taba siffantashi a dukka hasashenta dashi ba,sai ta janye idanunta daka kaf sashen da yake tana jin wani bala'e'en haushinsa yana sauka mata a hankali a hankali da wani yanayi me kama da tsanar mutum. Shine silar komai da komai,shine kuma maja ragamar kowacce kalar qaddara data sameta da kuma zata iya samunta a nan gaba. Tashi zuciyar kuwa ta cika da mamaki a yanzun da idanunsa ke sake haska mata qarancin shekaru qarara dake tattare da ita. Wani irin qyanqyaminta da wasarta suna nasar zuciyarsa. A wannan age din nata da duka duka idan tayi wuta bai wuce ace tana level one ba......amma s irin shekarun har take da fikirar SATA SANE FASHI DA MAKAMI TA YANAR GIZO.....abu mafi muni kuma shine KARUWANCI BIN MAZA. Wannan abu na qarshe daya tuna kadai ya sanyashi yaji zuciyarsa ta sake matsewa. Koda aboki ne dashi yake da dabi'ar neman mata......ba aboki ba,koda abokin kasuwancinsa ne kai muddin wannan din dabi'arka ce.....muddin kuma ta bayyana ya sani to yana haqura da huldar kasuwanci dakai. "Zunubinsa daban dude......haka mu'amalarku ma daban.....shi da Allah wannan halin nasa,baka da ikon canzashi" Kadan daga cikin abinda Farooq ke yawan gaya masa. Harara yake balla masa wani lokacin "Bani da sha'awar karbar kudi daga hannun ma'abocin sabon ubangijinsa,wattaqu fitnatalla tusibannal lazina zalamu minkum kaaassah(kuji tsoron fitinar da idan tazo bata shafar iya wadanda sukayi zalinci kadai a cikinku).idan kana neman albarka ubangiji cikin samunka....kayi qoqarin kaucewa masu saba masa,sai taka dukiyar tayi albarka". Irin maganganun nan sun jima suna fafatawa a kansu shida farouq. Ji tayi kaman jikinta na neman rasa duk wani confidence.....hakanan batason wanzuwa a muhallin da yake fesar da iska tana shaqa,sai taji kamar wadda ya fitar ita take zuqa,don haka ta juya a nutse da zummar komawa inda ta fito,tana ji har cikin ranta ta haqura da duk uzurin daya fiddota. "Ke!" Ta tsinci husky voice dinsa da bata taba jinta kamar haka a kusa kusa ba sai yau......karon farko kenan,wannan ya hadu da saukar tsawar tasa ya sanya gabanta wani mummunar faduwa.....kafin ta samu tayi hanzarin daidaita nutsuwarta da tattara dukka qarfin ta. Zuciyarta ke qarfafarta kada ta tsaya.....salon kiran da yayi mata din zallar raini ne.......yayin da ta nashi gefen ya fita hasala. Ya za'ayi ya kirata yarinya qarama irin haka tace zatayi ignoring nasa?,yarinyar da yayi imanin tsakanin musaddiq da saddiq ma babu sa'anta......koda ta girmi amna ma kuwa yayi imanin ba zata bata sama da shekara uku ko hudu ba. "Na rantse qafarki ta sake taku daya daga nan saina kakkaryaki na zubar" Ya fadi a hasale,saboda abinda tayi masan bazai tuna mutumin daya taba masa hakan ba tun sanda sunansa ya shiga duniya a matsayin muhammad fu'ad jadda. Batasan me yayi mata birki ba,har ta daga qafar zata taka step na farko saita mayar ta ajiye. Zuciyarta na mata wani irin suya a qirji. Ita yau sabreen wani d'a namiji ke kwatsawa tsawa har haka?,saboda kawai yana tutiyar ya aureta?. "Dawo ki zauna!" Ya sake fada a kausashe har sai da taji kaman yana daf da ita ne. "Ki sake na maimaita miki kuma....wallahi yau a cikin dakin karnuka zaki yini" Ya furta muryarsa na bawa me sauraro tabbacin da gaske yake. *_DUNIYATA LITTAFIN KUDI NE_* 08187255862 𝐃 𝐔 𝐍 𝐈 𝐘 𝐀 𝐓 𝐀 ̶B̶O̶O̶K ̶2 ⱧɄ₲Ʉ₥₳ 𝙋𝘼𝙂𝙀 17 18 Wasu maqalallun hawaye da bata tsammacesu ba taji suna tsatsafowa daga cikin qwayar idanunta,tayi hanzari da gaske ta dakatar dasu cikin bawa zuciyarta umarnin "Ba faduwa.......ba bada damar ganin lago.....i want to win". Abinda ya saka hawayen komawa kenan,saidai har yanzu tana jin alamunsu. Ta koma ko ta wuce abinta?,duk abinda zaiyi ma yayi?,ko kuwa ta zauna ya lissafa nasa qa'idojin itama ta sanya mishi nata iyakokin?. Bata tantance wanda zata dauka ba saiga kira ya shigo wayartata. Kallon wayar kawai sai taji tamkar wata sabuwar barazanar ce ta shigo cikin rayuwarta,sunan matar datayi saving dai still shi yake yawo. Abisa son ranta bata da Sha'awar sauraronta.....amma bisa tilastawar zuciyarta sai taji ba zata iya tsallakewa kiran ba,a sanyaye ta daga ta saka wayar a kunnenta. "Tun dazun nake zuba idanun ganin kiranki ai.....na dauka zaki nema taimakon abu na farko da zaki fara girkawa a gidan" Muryar maamah kenan da kalamanta na farko data fara jerowa baya ga amsa sallamarta da tayi. Idanunta data lumshe ya tilastawa boyayyun hawayenta saukowa,amma sai tayi hanzarin daukesu tana sauraren muryar matar. "Na manta na gaya miki wannan ko zasu taimaka miki wajen cimma nasara........yana da zafin rai.....yana da kafiya,bayason raini bayason musu.......bayason qazanta........kiyi duk yadda zakiyi ki zama ke kike ci dashi......ki sadaukar da komai masa......ki qarar da tunaninki kan duk hanyar da zaki maido cin abincinsa hannunki.......wannan shine kadai abinda zai sama miki 'yanci....." Saita dakata kamar me shirin bata damar cewa wani abu kafin ta qara "Idan kina da tambaya ko buqatar qarin bayani qofa a bude yake......zuwa anjima kina da baqi......saidai mutum daya ta qaru.....zan miki bayani a kanta.....af na manta na gaya miki.......dazu huda ta tsallaka shop din tsallaken titin gidanku fa". Mummunar faduwa gabanta yayi da ambatar sunan huda kawai a bakin maamah... Da gaske mutanen suke......sun mata tarko da 'yan uwanta,da gaske suke suna bibiye ne da rayuwar 'yan uwanta mahadin numfashinta?,da gaske kowanne motsi nasu a lissafe suke dashi?. Tabi maganar maamah ta tseratar da rayuwarsu?......a yanzu tana jin kamar shine babban haqqin daya zame mata dole ta sauke. Batasan ya iso wajen ba,kawai abinda taji shine zare wayar daga kunnenta. Ba qaramin firgita tayi ba,saita waiwaya da hanzari tana fuskantarsa sanda ya zubawa fuskar wayar idanu lokacin da kiran yake yankewa da sunan mariya b'aro baro akai. Ci gaba yayi da kallon fuskar wayar har sunan yayi disappearing yana sake maimaita full name din nata qasan zuciyarsa. Wani abu ya taso masa.......zarginsa yana daduwa daga kaso sittin cikin dari zuwa kasu casa'in da tara cikin d'ari. A nutse ya maida qwayar idanunsa kan fuskarta,haka kawai taji qafafunta sunyi laushin da kafin ya sake cewa komai ta koma ta zauna saman kujerar dake daura da ita,tana mamakin yadda nature da colour na idanunsa suka sauya kadan. Wayar ya cilla mata ta sauka daidai saman cinyarta,sai ya soke duka hannuwansa cikin aljihun wandonsa yana dubanta kai tsaye. "Kada ki dauka zakiyi duka irin rayuwar da kikaga dama,kada ki dauka zakiyi kalar rayuwar da kikeso.....kada kuma mi rudu da cewa kinzo nan gidan don ki huta......ki debi adadin kudi da dukiyar da kikeso daga jikin muhammad jadda.....idan kin dauki duka wadannan abubuwan a ranki......" Sai kawai wani siririn murmushi ya kubce masa,ya cije redlips dinsa yana dage kafadunsa sama ".......kina ruwa" Ya qarasa fada yana jawo wata ottoman chair 'yar qarama zuwa gabanta yahau kai ya zauna "Kisa a ranki nan kin shigo gidan tarbiyya da gyaran hali ne......gidan qare kukanka.......gidan bin daidai.......wadancan kayan duka da aka shigo dasu kin dauka a caca aka ciyosu?,ko kuma fashin yanar gizo da kutsewa account din al'umma akayi aka samosu da zaki bar komai cikin jakarshi?,salon idan ya lalace baki da asaran komai?" Wasu irin zafi sosai maganganunsa sukayi mata,irin zafin da bata taba kawowa ba. Ko mahaukaciya ce ita ta fuskanci inda batunsa ya dosa ballantana da hankalinta fes,zafin maganar ya tilastata daga oily eyes dinta masu sheqi dake shige da nasa ta kalleshi dasu. Duka girarsa ya dage sama yana dubanta da fuskar da babu digon walwala ko sassauci a ciki "Yes.......gidan nan dama komai da zai gilma a ciki zallar halak ce ta samar dashi.....so that bazan dauki almubazzaranci ba......dole ki kula da komai a daidai sanda ya dace da yanayin daya dace.....zaki zauna a cikinsa kiyi aiki irin na kowacce matar aure......zaki zauna a cikin gida kamar yadda musulunci ya tanada......zaki kuma zaman gyara halinki yadda zaiyi daidai da halin mataye na gari,ta yadda wataqila a gaba idan kin hadu da wanda kika dace da ra'ayinsa,zai dauki mace ta gari ba makwadaiciya me qarancin duka wata siffa me kyau ba.......". Banda sunansu huda,da zabin maamah dake mata amsa kuwwa cikin kwanya batajin zai fadi dukka wadannan kalmomin bata zazzage masa fiye da abinda ya gaya mata ba. Ba zata iya tuna cin mutuncinta da akayi a duniya da yakai wannan muni ba......cin fuska irin wannan a gaban idanunta,cikin salo na gadara da ganin isa. A nutse ta daga idanunta da wani irin coolness ta watsasu saman fuskarsa. Kallon kallo suka yiwa junansu na wasu sakanni,kowa da abinda ke gudana cikin zuciyarsa game da dan uwansa. Fuska ya sake tsukewa sosai ya dage dukka girarsa biyun "I told you.....your attitude needs a serious adjustment.......bazanyi tolerating any nonsense ba.....just obey all of my rules" Yana kaiwa nan ya miqe a nutse yana ajiye mug din sannan ya sake zuba hannunsa a aljihun wandonsa still yana kallonta. "If you have any plans i beg you kada ki fasa......if you collect some money or something else.....kiyi duk abinda kike ganin kin tsara" Yayi maganar wani abu yana taba zuciyarsa,zarginsa kuma yana sake qarfi a kanta da ganin sunan maamah kawai cikin wayarta. Wani mahaukacin bugun zuciya ya haifar mata,ba shiri ta sake daga kanta zuwa gareshi sanda yake barin wajen. Wannan karon kam duk qwarewarta wajen iya boye hawayenta abin ya faskara,fara tsiyaya sukayi kafin ta sake jin muryarsa yana fadin "Qarfe hudu akwai walima wajen anni......bana african time don ban sanshi bama.....i hope you get it" Ya sake fada ba tare daya waiwayeta ba. Kasa tashi tayi a wajen wani irin baqinciki yana nuqurqusarta. Tsantsar tsana da haushin maamah yana sukar zuciyarta. Bata qyale ire iren wadannan abubuwan.......ba abinda yake sakata sarewa ko fargaba,amma ta mata mugun qulli da dabaibayi da 'yan uwanta?,why?.....me su huda sukayi da zata sakasu a wannan wasan?,me yasa ba zata bari suyi tsakaninsu ba a nan zata fahimci wacece sabreen din....muhammad jadda......yana buqatar ta karanta masa karatun d'iya mace,if gana expecting taka kowacce mace don yana da dukiya da kuma kyau......zata so ta zama macen farko da zata banbance masa tsakanin aya da tsakuwa,amma a yanzun hakan kuwa zai yuwu?.....she needs to be very humble don ta kubutar da 'yan uwanta......but ba zata dauki raini wulaqanci da kuma cin fuska daga wajensa ba,wannan shine lokaci na qarshe da zata bari ya jera mata maganganu masu zafi irin wannan,zata saka dukkan effort dinta donta gamawa maamah aikinta cikin sati biyu ta kauce ta barsu da rayuwarsu su qarata,idanma gasashi zatayi ta cinye dukka damuwarsu ce.....itama nata familyn ta sani,zaman lafiyarsu da kwanciyar hankalinsu shine first priority dinta. A nutse ta miqe ta ta soma kauda komai badon maganganunsa ba....sai don da gaske bai kamata abar komai a wajen ya lalace ba. Neman abinci da samunsa abune me matuqar wahala wanda itace shaida akan hakan. Ta killace komai sannan ta tattara ta wuce zuwa dakinta,saidai qasan ranta cunkushe yake da wani irin bacin rai tare da lissafe lissafe masu yawan gaske game da yadda zata tunkari rayuwar. "Don't be sad.....kada ki takura kanki da yawa.....just live your life normally yadda ba zaki cutu ba" Abinda zuciyarta ta dinga nanata mata kenan. Akan idanunta biyu ta buga uku tazo ta shude aka doshi hudu. Bata dako niyyar shirin komai bare akai ga batun zuwa walima. Komai nasu baya burgeta......bata da buqatar kuma ta cudanya dasu sam sam. Daidai lokacin da yake samanshi bayan dawowarsa daga sallar la'asar. Yaga kira daga security din dake waje sun shaida masa yana da baqi gasu zasu shigo ciki. Tunda yaji haka yasan 'yan gida ne.....inda baqin fuska ne lallai saisun nema izini an basu kafin su barsu su shigo,sai ya qarasa shiryawa cikin shaddar daya dauko,don already wandon yana jikinsa kafin yayi receiving call din. Wagambari ce a jikinsa,asalin tsadajjiyar wagambari sky blue da aka yiwa wani irin dinki na alfarma dake nuna zallar zamani da kuma sanin darajar ado da dinki. Ba wani mutum da zaiga sutura a jikinsa ya sake ganinta ya maimaitata,kusan sakawa daya yakewa kaya ya gama dasu,shi yasa duk sati cikin fidda suturunsa ake. Gaban madubi ya tsaya yana karya hular da zai sanya,shi gaba daya a takure yake,ire iren wadannan sabgogin bai saba dasu ba kwata kwata,wani harkar taro na biki,idan kanason ganin karsashinsa kazo sashen maganar kasuwanci. Kayan jikinsa kansu nauyi sukeyi masa,baisan ma me yasa a kayansa na wannan watan aka hada masa da dinkin manyan riguna ba,amna daya tuna farouq sai ya tabbatar shirinsa ne kawai. Halfcover ya sakawa qafarsa dan qasar italy da akayi cinikinsa da dollars masu yawa. Ya sanya hular saman kansa take wani irin mutum.....lafiyayyen half cast ya fito me matuqar daukan hankali da kwantaccen kwarjini daka iya wucewa da zuciyar kowacce d'iya mace. Waya daya ya dauka kawai sannan ya soma barin dakin. Yana sauka ne cikin takunsa dake bayyanar da nutsuwarsa jin kansa da kuma kamun kansa irin na cikakken namijin daya hada abubuwa da dama. "Wow summa wow.....hammana" Muryar amna ta fara sauka a kunnensa sanda yake fitowa zuwa parlor din. Yadda tayi maganar ya sanya murmushi subuce masa,ta kuma tuna masa da lokutan baya da yake very free ba kaman yanzu ba. Kullum ita ke bawa kwalliyarsa mark,anni na zaune a gefe tana musu dariya,saddiq na tsokanarta wani lokaci harsu sanyata kuka,shike tare mata shine ke hanasu. "Hamma ka sake zama ango sak......don Allah BB farouq,kalli ta nan gefen" Sai datayi maganar ya lura da farouq dake zaune kujerar qarshe riqe da wayarsa yana dannawa. Kadan ya daga kai ya kalleshi ya maida ga wayarsa "Yayi kyau mana amna.....amma kubarni nima soyayyata nake qoqarin gyarawa......Allah bazan qara wata uku a qasa ba.....guy dinnan daga jiya zuwa yau kalleshi ya sake canzawa?". "Stop it farouq......" Fuad yayi saurin fadi yana duban amna kafin ya maida kallonsa ga farouq din. Ya fahimci sarai abinda yake nufi,akwai amna a wajen "Hamma........am eager to see my aunty wallahi.....where's she?" Ta furta alamunta na nuna da gaske sabreen takeson gani,tana jin qaunarta sosai har cikin zuciyarta saboda hammanta. "Jeki fito da ita" Ya fada yana yiwa amna nuni da hanyar. Bata ko tsaya sauraren komai ba ta wuce wajen da sauri saurinta. Qarasa takowa yayi wajen da farouq ke zaune bayan wucewar amna din,aje wayar farouq din yayi yana dubansa. "Mutumina......akwai labari kenan" Ya qarashe zancan yana kashe masa ido. Harara ya gasa masa "Gidan jarida na bude daga jiya zuwa yau baka sani ba?" Dariya sosai farouq ya tuntsire da ita. "Idanma hakanne Allah an maka uzuri.....da gaske ba wani abu sabo?,baka kawo kusanci tsakaninku ba?" "Kaga don Allah malam dakata" Ya fada da husky voice dinsa "Na gama gane inda ka dosa gaba daya fa.....na gaya maka ne abinda yasa na kawo ta cikin gidan nan kenan ko kuwa?,ko bunsuru ne ka aje?...." Dariya sosai ta qwacewa farouq fiye da dazu,yayi qasa qasa da muryarsa yana dubansa "Maganar gaskiya ban yarda dakai ba.....i know you kaima ka san da wannan......a hadaka da halal dinka gidan da ba kowa saikai da ita.....kuma kacemin bakayi filling distance din dake tsakaninku ba.....anya wannan kyan da naga kanayi zakacemin duka a banza yake?". Rasa me zaiyi masa ya huce yayi,sai kawai hannunsa ya fada kan remote din dake gefansa,ya shammaceshi ya wurga masa ya sauka a kafadarsa. Duk duniya farouq kadai ke masa irin haka,yana sake hararasa yana zura hannunsa a aljihu ya fiddo wayaraa Idanunta kawai ta ware daga kashingiden da take sanda taji ana knocking na qofar. Kashingidar da ta yita ne kawai tana tunanin abubuwa masu yawa tare da qoqarin cudanya abubuwan dake mata kai kawo cikin kwanya. Tunani kala kala ta dinga yi sanda taji ana knocking din.....shine ya biyota ya sake cin zarafinta ko kuwa?.....wasu ne suka sake zuwa gidan ko ko yaya?. Daga qarshe da taga bata da zabi dole ta motsa labbanta tana fadin "Waye?" "Nice adda....na shigo please?" Amna tayi tambayar cikin zaquwa. Kiran adda din da akayi sai ya sosa mata wani miki,mikin kewar 'yan uwanta wadanda su kadai ke kiranta da wannan sunan. Ambatar sunan ya sakata miqewa ta zauna sosai tana zuro da qafafunta qasa. "Shigo" Ta amsa kawai kai tsaye ba tare da tasan waye ba. "Assalamu alaikummm" Amna ta furta duka tare da shigowarta cikin dakin cikin murmushi tana riqe da handle din qofar idanunta akan fuskar sabreen yayin da fuskarta ke qunshe da wadataccen murmushi "Wa'alaikumussalam" Sabreen ta amsa mata tana mata duban rashin sani. "Ma sha Allah" Amna ta furta a sarari tana kasa dauke idanunta daga kan sabreen,murmushin saman fuskarta kuma ya kasa bacewa. Dama ta sani......ta sani tabbas hammanta ya iya zabe......tasan hammanta lallai zai zabo matar da ba irin ta kowa ba,amma bata taba tsammanin iya zabinsa yakai har kaman haka ba. "I know.....kece adda sabreen dinmu ko?" Tayi tambayar da murmushi sosai tana nunata da yatsa idanunta a kanta. Dan shuru sabreen tayi tana kallonta ba tare data iya amsa mata ba,kwanyarta na mata lissafin wacece wannan din?. Tana da surutu sosai da alama,amma kuma yanayinta kadai ya gaya mata me kirki ce. "Sunana amna hamza kibiya.....nice autarsu hamma fu'ad". Tayi mata bayani a taqaice saboda ganin yadda take mata kallon rashin sani. Ta fahimci sarai bayaninta......qanwarsa takeson cewa,kamar ta basar sai kuma wata zuciyar ta tambayeta "Meye laifinta ita?" Don bataga wani hali na daban tattare da ita ba duk da a yanzun ta fara ganinta,amma bahaushe yace alamar qarfi tana game qiba. Har amnan ta sare,sai kuma taga ta saki qaramin murmushi da yayi barazanar dauke hankalin amnan saboda yadda ya fidda kyawun innocent face dinta "Qaraso mana" Ta furta tana miqewa tsaye tare da komawa saman sofa bed". Dukka energy dinta ya dawo,ta tura qofar a nutse tana ci gaba da murmushi ta tako ciki tana samun wajen zama saman wata sofa din ta daban *_DUNIYATA LITTAFIN KUDI NE_* 08187255862 𝐃 𝐔 𝐍 𝐈 𝐘 𝐀 𝐓 𝐀 ̶B̶O̶O̶K ̶2 ⱧɄ₲Ʉ₥₳ 𝙋𝘼𝙂𝙀 19 19 "Am sorry aunty.....hala nayi disturbing naki kina hutawa" Ta sake fadi tana murmushi. Maida mata martanin murmushin tayi,wanda har sai da amnan ta furta "Ya salam,wanne irin kyau ne haka?". Kai ta girgiza "Ko kadan....." "Barka da rana,kin yini lafiya?,ya baqunta?,anni na miki ban gajiya,munzo mu wuce dake wajen walima......kowa yanaso ya ganki don jiya baku samu shigowa ba saboda dare ko?" Ta jero dukka abinda ke tafe da ita da wanda ke ranta kamar ba itace anni ta jawa kunne kada tazo ta cikata da surutu ba. A iya bayananta kawai ta gane wacece ita.....diyar matar nan da cikin kalamanta kawai zaka fahimci nutsuwa gami da tarin ilimi a ciki,wannan ya sanya sabreen sake sakar mata jiki kadan,saidai ta wani bangaren tana tunanin ta inda zata zamewa zuwa walimar,don sam bata shirya sake shiga kowanne taro ba. To na meye ma zata yita nuna fuskarta wa danginsu,bayan bawai tazo bane don ta zauna?. "Amma walimar......" Sai maganar tata ta katse saboda daga mata hannu da amna tayi sakamakon shigowar kira,tayi blushing kadan sannan ta kalli sabreen "Anni fa ba zama anyi suruka.....ungo nasan kirannan naki ne". Batason katsewa amna doki da farincikin da take ciki,don haka ta miqa hannu dole ta karbi wayar "Idan ba zaki samu daman zuwa ba diyata kada kiji kin takura.....kiyi zamanki,dama taro ne na sanya albarka,sai a sallami mutanen". Ji tayi ba zata iya mata haka ba,ba zata iya watsa mata qasa a ido ba,don haka tace a hankali "Muna hanya in sha Allah" "To Allah yayi muku albarka,Allah ya kawoku lafiya" "Ameen ameen" Ta amsa tana miqawa amna wayar idanunta nabin amnan da kallo. Ta fahimci wani farinciki takeji sosai,duk da batasan na meye ba,ganin amna din sai ya tuna mata da huda dinta,duk da ta girmi huda,saidai ita kuma ta girmi amna qila sa shekara uku ma ko hudu. Dole ta miqe ta soma qoqarin rage yafen jikinta da dankwalin kanta don shiga wanka,ta lullube jikinta da qaton towel ta wuce tabar amna tana bata labarin sabreen din,abinda yaso badda bacin rai da takurar zuciyar da take ciki ta shige bayi da boyayyen murmushi a qasan fuskarta. Komai na toilet din na kayan wankan ba irin nata bane,amna tunda ta karanta sunan products din da brand dinsu tasan harka ce kawai ta girma akayi. Daga yanayin sulbi da qamshin shower gel din kadai ta sake sallamawa,wannan ya dauketa minti kusan ashirin sannan ta gama. Towel biyu kawai ta shigo dashi,ta daura dayan,dayan kuwa dole ta nade kanta dashi saboda sumarta data jiqa da ruwa,ba wanda zata yafa don suturta jikinta,don haka ta sako shower slipper din zuwa bakin qofar toilet din ta cireshi saman water proof doormats din dake sashe na biyu na toilet din ta murda handle din ta bude qofar. Daidai lokacin daya soma duba agogo ganin sun sakashi dabi'ar daba tasa ba.....dabi'ar daya tsana ya kuma ja mata kunne a dazu da kada ta soma aikatata kwata kwata. Tsaki yaja ya fara lalubar number wayar amna,saidai ya kirata kusan sau uku bata daga ba,wannan ya sakashi miqewa a fusace yayi ciki yana cewa farouq "Ina zuwa". Takawa kawai yakeyi cikin hallway din ba tare da yasan wanne ne dakinta a ciki ba?. Haka ya dinga gota bedrooms din a hankali,sai daya isa na qarshe sannan yadan tsaya cak yana kasa kunne duk yasan bazaiji motsin komai ba saboda yanayin door din,a jikinsa kawai yaji da mutum a nan,sai ya juya yana fuskantar qofar ya murdata da dan zafin nama. Opposite suke tsakanin qofar toilet din dana shigowa dakin,wannan ya sanya kai tsaye kowanne idanunsa ya fada kan dan uwansa sanda qofofin suka bude lokaci guda. Budewar da taja hankalin amna wadda take zaune tana jiran fitowar sabreen. Sarqewa idanunsu sukayi lokaci guda......fuskarta tayi fresh sosai,glowing din nan da fatarta ta qara samu saboda gyaran data samu na musamman ya sake bayyana. Ruwan da tayi wankan dashi ya sabbaba tarwatsewar qwayoyin ruwan saman fuskarta,sai suma zame mata tamkar wani ado,musamman sumar gaban kanta data kwanta sosai ta kuma fito ta qasan towel din daya kimawa kanta don ta samu ya tsotse danshin da yake jiki. Ta sassannin dogon wuyanta duka wasu daga cikin sumar sun kwanta,sai suka zamewa wuyan nata kamar wani ado musamman kafadunya dake a tsaye da wani irin structure me daukan hankali da kuma tudu da zaunawar dukiyar fulaninta sosai a qirjin. Duka cikin qasa da second goma idanunshi suka kai wadannan. Wanda baikai mintunan da hankali da zuciyarka zasuyi zaton duka wannan karatun za'a iya yinsa a wadannan taqaitattun mintunan ba. Haduwar idanunsu na farko yayi mata ba zata,don bata taba kawo bayyanarsa cikin dakin ba,don haka ta maida qofar da wani irin sauri ta koma baya ta tsaya zuciyarta na wani irin bugawa. Idanunsa da yaji sunyi wani irin laushi ya janye daga bakin qofar yana tabe baki "Kamar gaske" Ya furta qasan zuciyarsa,zuciyar tasa tana ayyana masa Allah ne kadai yasan adadin mazan da suka ganta a hakan,tunanin daya sanya wani abu me ciwo ya tsaye masa a wuya. Wai wanne ma tsautsayin ya kaishi ajiye kayan da suke tamkar na kasuwa cikin gidansa?,zai iya killaceshi da gaske ya canza masa rayuwar da ta zame masa jini da tsoka?. "Ba damuta bane......damuwata na koya mata lesson ko saboda gaba......tasan ba kowanne kalar mutum kake tabawa ka kwana lafiya ba". Duban daya maida kan amna sai yaga itama shi take kalla.......daure fuska yayi tamau saboda ya karanci abinda ke fuskarta harda wani qunshe dariya "Karku kuskura ku wuce minti shida.....if not...." Sai ya nunata da yatsa kawai ba tare da yace komai ba ya juya ya fice yana tura musu qofar. "Adda......wallahi hamma ya tsani jira.....nasan kema kin sani,hurry up adda anni ma jira take" Muryar amna data sanar da ita ya fita. Wani wawiyar ajiyar zuciya ta saki,a hankali ta saki qofar data qanqame,sannan tabi hannuwanta da suke rawa da kallo. Da gaske ta tsorata,don tunda tazo duniya ba wani muharraminta daya taba ganinta a haka,wannan shine karon farko. Qoqari tayi ta hade hannayenta waje daya tana matsasu da kyau,sannan ta bude qofar sosai tana fitowa. Miqewa taga amna tanayi "Bari na baki guri adda ki shirya a nutse....." "Yi zamanki.....zan shiga dressing room na shirya" Tace da amna din,don idan ta fita ta barta fitowarta zatayi mata wahala.....infact ma zata iya canza shawarar zuwan. Tsaf ta shirya cikin wata doguwar riga ta atamfa bayan ta gama bulayin neman kayanta na gida,saidai ko ire irensu bata gani ba,sun lume sun narke cikin uban suturar dake danqare da closet dinta. Chantilly veil ta yafa daya dace sosai da atamfar jikin nata. Ta fito da wani irin kyau da kai tsaye bahaushe ke cewa qyallin goshin amarci.....saidai itakam ba days,tsabar gyaran jikin da tasha ne da kuma yadda ado ya zame mata jiki. "Tubarkalla ma sha Allah......tabarakarrahman......kiyi haquri adda inata tankaki.....i can't control my words ne wallahi". Murmushi kadan ta yiwa amna din,zuwa yanzu sai takejin kamar ta saba da halinta ne ma,tana da saurin sabo da shiga jikin wanda take so "Na gode" Ta fadi tana sanyawa qafafunta wasu high hill wanda kaman an yisu ne dama musamman saboda kayan jikinta. Kamar amna din ta mata magana amma sai ta bari kada sabreen din taga kama ta fiya rawar kai,a haka suka jero suna fitowa zuwa parlor din. Yayi relaxing sosai cikin kujerar kamar wanda bacci ke shirin dauka,saidai babu ko guda daya.....wata lafiyayyar kasala ce ta saukar masa tun daga fitowarsa daga cikin dakin. "Barka da fitowa sister" Maganar farouq kenan da taja hankalinsa,ya dauke idonsa daga email din da yake dubawa wanda duka ya raba hankalinsa gida biyu ne,daya kan ibtila'in faduwar darajar gold da diamond da suka wayi gari dashi......daya akan saqonninsa wanda kusan duka maganar dai daya ce,shirye shiryen bude company da yake tunanin jibi zai wuce abuja saboda baqinsa da yake kyautata zaton zasu fara sauka. Farat daya ta gane muryarsa,kaman amna shima sai take kirkinsa ya lullubeta,bawai murmushi tayi ba,amna ta sassauta fuskarta sosai suna gaisawa. "Ya kwanan baqunta?" "Alhamdulillah" Ta amsa masa itama tana rufe handbag dinta data jefa wayarta a ciki "Ma sha Allah....Allah ya bada zaman lafiya,ya baki ikon riqeshi" Yayi maganar yana maida dubansa ga fu'ad. Ko wajensu baya kalla tun duban farko da yayi musu bayan fitowarsu. Batace komai ba sai amna da tayi murmushi me sauti "Dude.....muje ko?" Farouq ya buqaci hakan "Kuje kai da amna.....gamu nan fitowa" Ya bashi amsa bai ko daga kansa ba. "Alright" Ya amsa masa yana daukan gorar ruwan da fu'ad din ya fito musu da ita yayi gaba amna na biye dashi. Shuru ya shude a falon na kusan mintuna biyu,bata ce kanzil ba kaman yadda shima baice ta tafasa a sauke ba,kowa yana ji da tashi izzar da girman kan. Ji tayi ta dauki iya adadin tsaiwar da zata iya.....ba zata dauki wannan halin nashi sam sam ba,don haka ta juya ta fara motsawa da zummar barin wajen "Hey!....Waye ya baki izinin tafiya" Ya fada da boldness cikin muryarsa. Abun taji ya mata wani iri.......wani baqon abu guda daya cikin rayuwarta. Batasan namiji yayi mata tsawa ba saidai ma ya lallasheta......batasan namiji yayi mata umarni ba.....a kullum ita ke basu umarni.......ba'a keeping dinta ta jira mutum saidai shi yayi jiranta koda awanni nawa tayi nufin qararwa a wajen. *DUNIYAT LITTAFIN KUDI NE(PAID BOOK)* 08187255862 𝐃 𝐔 𝐍 𝐈 𝐘 𝐀 𝐓 𝐀 _ZAFAFABIYAR_ ̶B̶O̶O̶K ̶2 ⱧɄ₲Ʉ₥₳ 𝙋𝘼𝙂𝙀 20 20 Tana tsara komai a sanda takeso a kuma yadda taga dama......kuma a bita a hakan. "Kina tunanin hatta dressing naki zakici gaba da yinsa yadda kika saba?......idan nace komai naki zai canza ina nufin komai din......ciki harda shigar da bata dace ba.....bata kuma yi ba,ki kalli amna.....kin ganta da irin wannan useless mayafin?". Iska sosai ta shaqa har cikin ranta tana jin wani zafi.....abinda yakeyi matan wasu abubuwa ne da babu d'a namijin da ya taba yi mata shi sai shi. Sai taji haqurinta ya gaza jurewa......don haka cikin muryarta me nuna bacin rai tace "Kana zaton baiwa ce daka shiga kasuwa ka siyo?......meye alaqarka da dressing dina?". Maganar tata ta sakashi gyara zamansa sosai. Yadan jijjiga kai "Kin shirya wasan kenan kema?.....musu?,taurin kai.....abubuwa biyu da nafi tsana a rayuwata" Yayi maganar yana kada yatsunsa guda biyu idanunshi akanta duk da baya iya ganin fuskarta "Bauta.....meye marabar dambe da fada?.....kina tunanin kudin da kika sacemin kimar kudin aurenki sunkai yawan haka?......banajin kinkai tsada haka.....well,ba wannan ba,ki shiga ki sauke wannan banzan mayafin ki saka sutura sosai a jikinki......karki bari na maimaita maganata......i hate it". Cak maganan ta tsaye mata a rai,wani irin bacin rai ya taso mata. Wannan ya sanya da sauri sauri ta fara yin gaba,don tanaji muddin taci gaba da tsaiwa a wajen zai iya gano lagon fushinta,abinda kuma taci alwashin ba zata taba bashi dama a kai ba. Ci gaba da birkita closet din tayi bangaren veils cikin bacin rai,gaba daya veils din taji basu yi mata ba,sai kawai tahau tube kayan,ta kwabesu tas ta fara neman wasu daban. Turkey dress hannunta ya fada kai,cikin shigar da tafi so kenan,sai ta fara shirya kanta cikin turkey abaya din wadda cikin qanqanin lokaci ta rufe mata jikinta ruf,ta kuma fiddo da kyakkyawar baby face dintannan. Haka kawai sai taji tafijin dadin shigar,duk da dama tun asali ita din bata iya shigar bayyanar da tsiraici ba.....kawai dai Chantilly veil yana cikin veils din da tafi so,kuma ko a yanzun ba zata bari ya rabata dashi ba. Motsin tahowarta ya sakashi daga kansa a nutse. Duba daya yayi mata ya kauda kanshi,sai ya miqe yana ficewa tun kafin ta qaraso. "Ya Allah......wai BB don Allah a ina hamma ya samo adda?" Amna data kasa daurewa sanda ta hangi sabreen na takowa zuwa inda motoci ke jiransu ta fada. Iya takunta kawai saika dauka rausaya ko kuma yanga takeyi ta cikin hill shoes din data sakawa qafafunta masu igiya. "BB.....wai dama hamma shima yana kallon 'yammata don Allah?". Boye dariyarsa farouq yayi,don sarai yaga isowar fu'ad wajen amma bai nunawa amna ba "Me yasa kika ce haka?" "To ai......hamma fa kaman horror yake......ina noticing nasa duka shekarun nan,Allah saiki wuce ta gabansa amma baisan wacece ke ba......to amma ya akayi idanunsa suka kai kan addana me mugun kyau haka?" "Yaushe kika zama gulmammiya amna?" Farouq daya kece da dariya ya fada yana satar kallon fu'ad dake tsaye kawai ya kasa cewa komai. Dariyan itama takeyi "Allah BB......ban taba ganin mutumin daya iya zaben mace ba irin hammana......da gaske hamma ya hadu tako ina,komai nasa ya banbanta dana kowa" Ta fadi hankalinta kwance batasan yana a wajen ba. Zabura ta danyi da jin gyaran muryarsa,tsaf ta dinke bakinta tana raba idanu "A nan za'ayi walimar ne?" Ya fada yana jifan farouq da wani irin kallo na zaka sani ne. Dariyarsa ya yiwa control yana fadin "No.....aike muke jira,ko ka manta kaika koromu waje zakayi ganawar sirri da madam" "Enough" Ya fada yana tura masa murfin motar kaman zai bugeshi cikin nuna alamun ka soma wuce gona da iri. Hakan shi yayi masa,don haka yaja murfin ya rufe yana gaya masa shi da amna zasu tafi a nan. Baibi ta kansa ba ya nufi ainihin motarsa qirar Mercedes Benz G400d baqa wul daketa daukan idanu wanda haka ke nuna sabuntarta da kuma kalar kulawar da take samu. Da sauri daya daga cikinsu ya bude masa,kai tsaye ya wuce ya zauna sosai idanunsa na sauka a kanta. Ya tsani jira sosai,baisan me yasa take tafiya kaman ba zata qaraso wajen ba,bayan ya tabbatar taga inda ya shiga. _wataqila da wannan take sake samun damar yaudarar maza_ tunanin daya d'arsa masa a rai kenan,wanda ya sake sanya mishi qyamarta ainun,har yakejin kamar ma bazai iya hada numfashi da ita cikin mota guda ba. Ba zata bari ba ba kuma zata sake tayi wani abu na zubewar kimarta da mutuncinta gaban guards dinsa ba,wanda dukkaninsu haushinsu takeji. Bataga meye dalilin da zai zube qatti irin wadannan suna kewaye dashi ba kamar tsohon barawo ko wanda yaci kayan wani ba(a iya nata sanin na iya tsaron daya zama dole me harka irin nashi ace ya samu),me yasa bazaiyi rayuwa normal irin ta mutane ba?,da wannan kalar tasa rayuwar kenan itama yakeso ya tursasata ta zama haka?,tayi rayuwa irin nashi?,bazai yiwu ba kuwa. Daidaita zamanta tayi sannan aka maida murfin motar aka rufe mata,sai motar ta dauki shuru sai sassanyan qamshinsa daya danne nata,har ya zamana duk wani numfashi da zata shaqa tare da qamshin nasa yake zuwar mata hunhunta. Tsaki ta saki a boye yadda bazai ji ba,ta maida kanta daya window din da take zaune daura dashi. Batasan sun fara tafiya ba sai da taga motar ta fara sulalawa tana nufar makeken gate din gidan suna gilma shukokin da aka qawata wajen dasu. Basuyi nisa ba kira ya shigo masa,wanda shi ya zame masa abokin tafiya. Duka maganganun cikin harshen turanci yake yinsu da wani irin accent dake nuna zallar qwarewa gami da gogewa a yaren. Kusan fin rabin maganganun nasa ba wani fahimtarsu takeyi ba,don zuciyarta tayi nisa da wani tunani na daban. Ta wani bangaren kuma yadda yake lanqwasa harshensa ba kowanne word take ganewa ba a matsayin karatunta na wadda ya dakata daga aji biyar biyu na babbar secondary wato senior secondary school. Sanda motarsu ke qoqarin cusa kai ta cikin babbar gate din dake da wani irin girma da kuma jan hankali,a sannan ne ya katse wayar ba kuma don ya gama ba. Ya kashe wayar gaba daya tana kallonsa ta gefen idanu,ya zurata cikin wani dan abu daya matsa ya fito ya saka wayar ya koma ciki. Adan qaramin zamansu na mintuna ta karanci abubuwa daban daban tattare dashi,kusan kaman komai nasa na dabanne kuma daban yake,saita tabe baki sanda suka isa babban parking lot na alfarma da gidan ya mallaka. Qasa tayi da kanta tana jan mayafin data lullube kanta dashi sanda take hangar wasu mata suna bullowa daga wata qofa da tafi kusa da parking lot din,kafin takai gayin komai amna ta bayyana ta kama murfin tana budewa,abinda ya bata daman jin maganganunsu. Muryar amna ta fara ji "Inna uwaisha......ga addan namu.......ku fito mana da ita a hankali" Ta qarasa fada tana qaramar dariyar dake nuna zallar farincikinta "Kinyi qoqari auta sannu.......kin gama naki" Wadda aka kira da uwaisha ta fadi tana matsowa gaban motar "Kamar gaske" Sautin muryarsa ta fita a hankali ya furta sanda kan sabreen ke qasa tana jin wani fargaba haka kawai na haduwa da mutanen da batasan su kuma meye nasu kalar halin ba,sunan auta da taji an ambata sai ya sanya duka tsigar jikinta ya tashi,haneefa da tun da safe take kokawa da tunaninta ta fado mata.....ko yaya ta wuni?. "Zallar karamci da girmamawa da mutuntawa muke gabatar miki" Abinda inna uwaisha ta fada kenan kamar tasan abinda sabreen ke wassafawa qasan zuciyarta. Miqa mata hannu inna uwaishan tayi tana fadin "Sauko a hankali nayi miki jagora zuwa ciki,ki shirya don kowa na dokin jiranki". Bata musa ba ta sakawa inna uwaishan hannunta "Fatabarakallahu ahsanul kaliqeeen......da iya lallen nan ma kawai an tashi kaina yallabai". Inna uwaishan ta fada tana dariya dariya idanunta akan muhammad fu'ad dake qoqarin ficewa a motar sannan ta maida dubanta ga amna data dage mata gira alamun Yes. Inna uwaisha na daya daga cikin makusantan anni da suka daukeshi tamkar d'a,duk da cewa tana da jika qwaya daya amma idan kaga suna raha da amna saika dauka yaya ce da qanwarta,hakanan suma ta daukesu duka mazan gidan. Bai iya cewa komai ba,sai dan motsawa da labbansa sukayi alamun murmushin dole kawai ya sanya qafafunsa ya fice daga motar. Kunnuwanta kawai ke iya jin surutansu amma idanunta suna a rufe. Batasan ina suke nufa ba saidai idanunta na iya kallon lullubabban luxury marbles din dake shimfide a wasu sassan na gidan,a haka taji sun isa wani daki da a nan inna uwaisha tace da ita "Fell free sabreen.....ki shirya amna zata tsaya dake,idan kun kammala zan dawo mu wuce wajen taron,kowa ke yake jira". Kai ta gyada a hankali,cikin ranta kuma tana zancan zucin wanne shirin kuma zata sakeyi bayan na jikinta. Sanda amna ta gabatar mata da komai na shirin shuru kawai tayi tana bin kayan da kallo......shin da saninsu wanne irin aure ne akayi suke wahal da kansu haka da kashe kudade da hidima?,ko kuwa kallo kawai sukewa abun irin duban bangon littafi ga idanuwan da basusan meye a cikinsa ba. Wata lafiyayyar Moroccan gown dake da wani irin ado na daukan hankali......saidai kuma duk da adonnan nata sam bata da nauyi ko kadan. Hade take da wani irin hijab dan qarami da yafi mata kama da na Indonesia ko Malaysia.....a ciki batasan wanne ne ba. Komai na kayan fari ne qal da wani irin haske me daukan hankali. Ita kanta bayan ta gama shiryawa batasan lokacin data dauka tana kallon kanta ba,sai take ganin kamar ba ita ba.....duk da kusan komai ma yana zuwa mata ne da wani irin ba zata da bata taba zato ko kawowa cikin rayuwarta ba. Amna ce ta fara shigowa wadda fiye da dazun a yanzunma ta susuce wajen yabawa sabreen din. "Inna Allah kwanan nan hamma zai manta da wani gold da Diamond" "Maza dai ya jiki" Inna uwaisha ta fada tana riqe hannun sabreen suna nufar qofar fita. Suna shiga wajen tasan sun iso,duk da kusan kowa na zaune a nutse ana sauraren jawabi daga bakin malamai. "Muna yiwa amarya barka da shigowa". Maganar data dauki amsa kuwa cikin hall din,ta kuma bawa maamah damar fara gyarawa tsaf don bayyanar da kanta a wajen. Ringing biyu wayar tayi ya daga yana sakata a kunnensa "Ya kamata ka qaraso wajen walimar fa.....akwai mutanen da zaku gaisa dasu" "Bana kusa" "Kaman yaya?" Farouq ya tambayeshi a mamakance "Eh.....kaman yadda kaji bana kusa,uzuri ya kamani nadan fita" "Why.....you know......" "Anni zata fahimceni idanma kai baka fahimta ba.....sai na dawo" Ya amsa masa yana katse wayar ya maidata ya ajiye. Shi a yanzun kasuwancinsa shine abinda yafi damunsa shine kuma gaba da komai,bai takurawa kowa ya matsawa kowa ba,don hatta da saddiq daya Kamata ace a yanxun suna tare suna duba al'amuran da suka taso musu bai masa magana ba,bai kuma ce komai dashi ba saboda yaga ya sanya kanshi cikin hidimar bikin sosai,ya bashi lokaci ya qare ya dawo hayyacinsa.....tafiya ce dai dasu tsakanin jibi da gata,kuma bazai dage masa qafa ba dole ya shirya su wuce. Girgiza kai kawai farouq din yayi,halin fu'ad saishi,baisan ma yaushe ya fita din ba bayan sun shigo cikin gidan tare. Ya sanshi sarai ya kuma sani,wani irin mutum ne shi da kasuwancinsa ke gaba da komai idan ka dauke shi anni abba da su saddiq,amma koma meye yana ji a jikinsa,yana Kuma fatan duk yadda yakai ga gujewa auren da bashi wani rashin muhimmanci ya zame masa silar shiryuwa da saituwa kaman kowanne magidanci. A nutse farouq ya ratso cikin mutane ya yiwa anni rada. Kai kawai ta gyada sanda idanunta suke kan sabreen dake zaune waje daya bata ko qwaqwaqwaran motsi. A iya haka tana iya hangen nutsuwa a tare da ita,sannan haka kawai takejin qaunar yarinyar cikin ranta. Tana iya hangen wasu abubuwan ta cikin mayafin dake lullube saman kanta,a sanda walima tayi nisa..... Kai kawo na mutane ya qara yawa tata zuciyar cike take da lissafe lissafe kala kala. Lumshe idonta tayi sanda aka fara gabatar da miqa gudunmawa ga amarya,wato kowa zaizo ya zube mata tasa gudunmawar adan wani babban qwarya dake ajiye a gabanta maimakon yin liqi,wanda daga nan za'a fara gabatar da lectures akan zaman aure. Numfashi ta sauke daga can cikin hunhunta,duk cika da batsewar mutanen dake a wajen bata hangi wani nata ko mutum daya ba. Sai takejinta bare a wajen da wani irin rashin sukuni da takura. *DUNIYATA LITTAFIN KUDI NE(PAID BOOK)* 08187255862 𝐃 𝐔 𝐍 𝐈 𝐘 𝐀 𝐓 𝐀 _ZAFAFABIYAR_ ̶B̶O̶O̶K ̶2 ⱧɄ₲Ʉ₥₳ 𝙋𝘼𝙂𝙀 21 21 A nutse aka fara zuwa daya bayan daya ana zube sabbin 'yan dubu dubun fil a miqe cikin bundles dinsu a gabanta. Ta rasa tsakanin burgewa da rashinsa wanne takeji cikin zuciyarta?,duk da ta hangi tarin nutsuwa da kamala a komai na taron. Idanunta ta sake dagawa a hankali ta cikin mayafin tana kallon bakin qofar shigowa gurin dake facing dinta......tamkar abinda ake jira kenan saita hangi huda na shigowa. Da farko ta dauka kaman gizo idanuwanta sukeyi mata ko kuma me kama da ita ne,saidai shigowar nadra da haneefa ya qarasa kore mata dukka shakkun data soma ji cikin ranta. Wannan bai saketa ba taga abinda ya kusa doka zuciyarta saboda firgici.....maamah ce.......tana biye dasu da dukkan alamun da zasu gwada maka tare suke......tare suka shigo,don waiwayawa haneefa tayi da alama kiran sunanta tayi,sai taga ta riqe hannunta haneefa na mata murmushi tana maida mata sukaci gaba da takowa wajen tare. "A ina ta gansu?,a ina ta daukosu?,ya akayi taje ko sukazo wajenta?,tun yaushe?,me kuma take gaya musu?" Tayi tambayar sanda taga ta tsaidasu duka su ukun kuma kowacce ta tattara mata hankalinta. Sanye take cikin wata 'yar ubansun super embellished me asalin tsadar da jikinta ke bada wani irin santsi tamkar ba atamfa ba. Tun daga yanayin shigar zaka tabbatar da gaske ta dauki duniyarta dama rayuwarta gaba daya.....hakanan da gaske komanta yana mata dadi yana kuma tafi mata yadda takeso. Daga bayanta hajja harira ce data shirya kanta itama cikin applique lace ruwan sararin samaniya. Ita dinma duba daya zakayi mata ka tabbatar da halin yazo daya kamar yadda abotar tazo daya. Kai tsaye ta daga yatsa tayi musu nuni da kujerar da sabreen ke zaune a kai,sai dukkaninsu suka maida idanuwansu kanta. Fuskokinsu suka cika da farinciki duk da basa iya ganin fuskarta sosai,suka motsa kamar zasu taho zuwa wajenta,amma sai taga ta sunkuya tana magana dasu. Cikin qasa da second talatin taga sun maida hankalinsu gareta.......sun kuma juya suna binta a baya zuwa hanyar data nufa,daidai lokacin da me gabatarwa ke bada sanarwar "Mahaifiyar ango ta shigo......uwarsa kuma zata marabceta" Maganar data finciko hankalin sabreen daga shingen tunanin data afka sanda take binsu da kallo suna biye da maamah sau da qafa.....kai kace ummeensu ce ta dawo duniya. "Uwa?.....mahaifiya?,wacece?" Ta samu kanta da shiga wannan rudanin tare da fatar a yau ta samu warwarewarsa,don haka ta buda dukka idanunta tana bin kowanne kusurwa da kallo tanason samun warwarar rudaninta. Cikin nutsuwa da girmamawa anni ta miqe tana dosar inda maamah ke a tsaye,fuskar annin shimfide da fara'ar data ratsa har qasan zuciyarta. Har yanzu gangar jikinta da ruhinta basu daina jin farinciki da alfaharin aurar da fu'ad ba......wani abu guda daya daya zamewa maamah tamkar dafi tsakiyar tsokar zuciyarta "Ameenatu ce ta aurar dashi" Kalmar da inda tana da ikon gogeta tsaf saita gogeta daga dukkan wata ma'adana ta kalamai. "Barka da zuwa......sannunku da zuwa......" "Uwa kuma mahaifiyar muhammad fu'ad jadda ba,ai haka ya kamata ne gabatarwarki ta fadi" Hajja harira dake tsaye gefan hannun hagun maamah ta furta da wata irin izza. Kallo daya anni tayi mata ta watsar da ita gami da bawa banza ajiyarta,idanunta suna sauka akan fuskar 'yammatan su uku da take ganin tamkar ta taba ganin fuskar a wani waje. Kallonsu kawai tayi suka fara gaidata daya bayan daya,ta amsa musu tana dafa kan kowaccensu da madaukakiyar fara'a da kuma kulawa,kulawar da ta sauka har cikin idanun sabreen wadda ruhinta gaba daya yana a wajen,saidai babban qalubalenta bata iya jin me aka tattaunawa akai. Tun daga tashin anni har tsaiwarta a wajen sabreen na tuna guraren data taba ganin fuskar matar ne. Indai da gaske itace anni......itace uwa ga fu'ad ba shakka ta santa......amma ta yaya haka ta kasance?,ya akayi yake da uwaye biyu?,me yasa anni data taba sani duk da alkhairi ya hadasu ba ita ta nema masa ita ba?,sai waccar baquwar fuskar da bata taba ganinta ba kafin faruwar wannan abun kaf tsahon rayuwarta?. "Barkanki kade Ameenatu.......sannunki da hidima" Maamah ta maida mata da wani irin salon murmushin da ya sanya anni tajishi har cikin jinin jikinta. "Ina tayaki murnar aurar da fu'ad da kika samu damar yi......wannan babbar dama ce da zata zame miki tarihi kuma abun tunawa watan watarana.......ina aka tanadarwa mahaifiyar fu'ad domin ta zauna ita da qannen matarsa?" Tayi tambayar kai tsaye cikin isa...... "Ai albarkacin kaza qadangare kansha ruwan kasko mariya....muhalli har sai kin baiwa wani" Anni ta fadi duk da rabin hankalinta yana kan yaran abubuwa masu yawa suna yawo a ranta. Waiwaya tayi ta yafito muhsina inna uwaisha dake shirin wucewa "Itace mariya.......a cikata da irin karamcin nan da aka gada,koda zata cika hall dinnan da jama'arta.....a tabbatar an gamsar da buqatarsu,a nuna mata dattako da dattijantaka" Dukka anni tayi maganganun da kai da bakasan komai ba zaka dauka zallar magana ce kai tsaye,saidai gasu hajja da maamah din dukkaninsu sunsan magana ce akayi musu me harshen damo. Juyawa abinta anni tayi tana komawa cikin jama'arta,maamah tabi bayanta da kallo tana jin zafin jirwayen datayi musu me kama da wanka. Zafafan baqaqen maganganun data fahimci kowaccensu,amma kuma saiga murmushi yana subucewa daga saman fuskarta "Kwanaki kadan suka ragewa izzarki ameenatu.....na rantse koda pant din dake jikinki da kudin muhammadu aka siyeshi saikin zareshi kin miqomin.......na rantse sai na sanya fu'ad ya gaya miki maganganun da zasuyi silar ajalinki......maganganun da zasu zame miki dafin da zuciyarki zata buga ta tarwatse pieces " Tayi dukka maganganun ita da zuciyarta tana me cike da alwashi. Duk da wadannan abubuwan data samu ta kuma aiwatar zuciyarta ta kasa samun nutsuwa ko qanqani.......sam farincikinta har yanzu rabi ne......daga sanda ta iso bakin qofar mansion House din Alhaji hamza kibiya duka sai taji ta raina nata gidan kwata kwata. Batajin akwai wani gida ko gini da fu'ad zaiyi mata komai kyau da dukiyar da aka narkar ya zauna mata a rai muddin zai zamana muhallin Alhaji hamza kibiya yafi nata......indai zai zamana matsugunnin ameenatu zai d'ara nata. Daina fahimtar komai tayi......daina fuskantar duk abinda ake gudanarwa tayi,dukka idanunta dama hankalinta suna kan 'yan uwanta,suna kan kowanne motsi da kai kawo nasu. Hankalinta taji yana tashi,bata qaunar kowacce mu'amala ko alaqa kome qanqantarta tsakanin maamah dasu,saidai yadda taga tana jansu a jiki,ta wani.mugun sake musu ko ita batajin ta sake musu haka. Haneefa duk girmanta tana saman cinyarta tana wani lallabata,irin lelen da haneefa din keso a matsayinta na auta take kuma qishirwarsa. Cafko hannun amna tayi wadda ta zuge tata jakar ta fara fiddo sabbin 'yan dubu dubu kaman ba'asan ciwo da zafinsu ba.....kamar ba wasu abu masu muhimmanci ba tana zubewa sabreen din. "Kiramin su nadra.....kice suzo yanzu yanzu injini". Dubanta amna tayi duk da bata iya ganin fuskarta sosai. "Su waye?" Ta tambayeta don bata gane ba. Ajiyar zuciya ta sauke tana qoqarin saita kanta,sai sannan ta tuna amna din bata sansu ba "Sun shigo yanzu su da......." Ta dakata tanason tuna sunan da ake kiranta dashi "Su da maamah" Kai amna ta daga tana hangensu daga nan inda take,kwata kwata bata qaunar abinda zai hadata da matar,bata qaunar kallon da take binta dashi irin kallon dake fita daga idanuwanta zuwa kanta,amma zuwa aiken sabreen ya zame mata dole "Okay" Tace da ita "Na gode" Sabreen ta fadi da sauri saboda jin dadin zatayi mata abinda takeso a sanda bata da damar tashi. Da ido take bin amna sanda take nufarsu,duk wani taku dake qara kusancin ama dasu bugun zuciyarta qaruwa yakeyi,ta kasa dauke idonta daga kansu daidai da second guda har zuwa sanda ta qarasa gabansu. Taga amna ta mata magana,ita kuma ta waiwaya tayi magana dasu kafin ta sake dubanta still ta gaya mata wani abu daya sanya amna din juyowa ta dawo mata. "Me suka ce?" Ta fara da tambayar amna din tun bata gaya mata komai ba "Zasu zo.....zasu taho tare da maamah din wai". Idanunta ta maida ta lumshe tana girgizawa amna kai kawai. Wani irin rikitaccen yanayi yana sauko mata,kada dai ace suna jin wani sauyi na daban akan maamah kamar yadda takejin wajabcin bin umarninta tako ina yana ratsata?. Tun daga wannan sa'ar nutsuwa tayi mata qaura,ta kasa debe idanunta daga kan 'yan uwan nata,duk wani motsi murmushi da kuma fara'ar fuskarsu ya tabbatar mata suna jinsu ne cikin sukuni da farinciki,har zuwa lokacin da aka bada sanarwar isowar mahaifiyar ango zuwa inda surukarta take. Tamkar mejin tsoron wani abu haka zuciyarta taci gaba da bugawa sanda maamah ke kusantota tana takowa wajenta dasu nadra gaba daya. Idonta ta lumshe da sake budesu akansu gaba dayansu tana me kyautata zaton saisun iso gareta ne kai tsaye kafin aiwatar da komai......saidai kuma akasin haka ne ya faru. Kamar kowa suma wajen zuba kudin suka nufa,kowacce ta dire rafas na dubu dubu sabbi guda uku dake hannunsu huda kuma ta zuba biyar. Bin kudin tayi da kallo,suka kuma tsaye mata a rai. "Wai ina momma bahijja?" Tambayar da bata da amsarta batasan kuma wanda zai gaya mata amsar ba. Ta tabbatar daga kansu har zuwa momma ba wanda zai basu wannan kudaden son suzo su zuba a wajen.....amsarta ta fito sanda maamah ta cire wani rafas din ta bawa nadra da zummar ta qara a ciki. "To kuje ku gaisa" Maamah ta basu umarni sanda ta fara zube nata kudaden da suka ja hankalin mutane da dama. "Waye ya kawoku?, yaushe kukazo?,ina momma?" Ta damqe hannun nadra da tafi kusa da ita tana jera musu tambayar a gaggauce daya bayan daya. "Momma ta tafi yau....tun da safen mukazo,mun dawo gidan maamah......" "Tana da kirki adda.....kuma tace kema kina nan,zamuci gaba da ganinki.....kayanmu ma tace basai mun taho dasu ba......kawu yace muyi zamanmu zamufi samun kulawa". "Baki da hankali huda?" Ta fada da sauti me qarfi tana qoqarin janye lullubinta don ta samu damar saka idanunta cikin na huda. "Yi a hankali......idanun jamaa suna kanki" Maamah data sunkuya saman kanta tana maida mata lullubinta ta fada da murmushi akan fuskarta kamar wani abun arziqi take gaya mata. "Ku tafi mu zauna daughters" Ta fada da kulawa sosai a muryarta da cikakkiyar fara'a. Tana jin takunsu sanda suke sauka a wajen,ba damuwa ko wani abu cikin muryoyinsu,tana jin tafiyar nasu na buga zuciyarta sosai,tanaso qwalla ta fita daga idanunta komai qanqantarta ko zataji sanyi,amma ko daya bata samu wannan damar ba. Koda aka kirayi anni saita aike amna da wani qaramin akwati da ba wanda yasan meye a ciki aka ajiye cikin wani salo na siyan girma. *DUNIYATA LITTAFIN KUDI NE(PAID BOOK)* 08187255862 𝐃 𝐔 𝐍 𝐈 𝐘 𝐀 𝐓 𝐀 _ZAFAFABIYAR_ ̶B̶O̶O̶K ̶2 ⱧɄ₲Ʉ₥₳ 𝙋𝘼𝙂𝙀 22 22 Kafin a tashi tsaf ta rasa sauran nutsuwarta,wani irin tashin hankali takeji maras misali daga kowanne lungu da sashe na zuciyarta. Ba abinda ke gilmawa ta idanu da zuciyarta sai huda nadra da haneefa......ina momma bahijja?.....ina momma bahijja?,.....da gaske ne sun bawa maamah yaran?,ya akayi haka ta kasance?,ya akayi ta tafi ba tare da sunyi sallama?,ya akayi ta tafi ta barsu bata cika mata alqawarin data dauka akan 'yan uwanta ba?......zata sakene ta kalli rayuwarsu ta balbalce?,ko xatayi dukkan abinda ya kama tayi don ta tseratar da rayuwar yaran?. Wadannan sune tambayoyin da ta dinga yiwa kanta har a sanda take cikin kebantaccen qaramin parlor din da amna ta kawota bayan tashi daga taron,tace ta zauna zasu gana da anni. Dogayen yatsunta da suka sha lalle kawai take murzawa kanta a qasa,zuciyarta na wani irin zafi tare da jin qaguwar su koma gida ta lalubi maamah suyi magana ta sosai da ita.....koda tana jin kamar ta samu ikon sarrafa zuciyarta da bin umarninta cikin wani irin takura da takeji ana yiwa zuciyarta,.....to amma sam bata samu lago akan abinda takeji a zuciyarta game da 'yan uwanta. Qaunarsu darajarsu martabarsu da kuma soyayya da shaquwar data ginu tsakaninsu ba abinda ya sauya. "Assalamu alaikum" Muryar anni ta ratsa falon tana murza qofar ta shigo "Wa'alaikumussalam" Tada daga kanta kadan tana duban qofar gami da amsa sallamar. Kallon kallo suka yiwa junansu,kowanne a cikin su yanason tuna inda yasan fuskar dan uwansa. Sabreen ce tayi saurin watsar da qoqarin lalubo inda tasan fuskar annin,saboda gaba daya hankalinta ba'a nan yake ba,sai ta samu kanta kawai da zamewa daga saman kujerar tana gaidata,wata dabi'a data manta rabon data aikatata,amma a yau ta samu kanta da yin saboda wani kwarjini da taji matar tayi mata. "Koma ki zauna abinki daughter" Ta fada da kulawa amma saita kasa hakan,saita samu kanta da zama sosai tana tanqwashe qafafunta. "Na tsaidaki ko?,ga dare yana qara yi,duk da me babban sunan bai qaraso ba,uzuri ya taso masa daya saka dole ya fita" Kai ta sakeyin qasa dashi ba tare da tace mata komai ba,batasan me yasa matar take mata kwarjini haka sosai ba. "Bari muyi magana a taqaice a gaggauce......da farko ina miki maraba da shigowa cikinmu da kikayi,ina fatan Allah yasa ku zama abokan arziqin junanku.....Allah ya hada hankalinku waje daya......bani bace mahaifiyar fuad,amma idan na kira kaina uwa a gareshi nasan banyi laifi ba,ni din uwar riqonsa ce tun daga quruciyarsa har kawo yau.....hajiya mariya wato maamah itace mahaifiyarsa". Dole bata shirya ba maganar ta sakata daga kai da hanzari ta dubi anni,sai kuma ta maida ta sunkuyar "Baiyi sa'ar uwa ba.....ke kuma bakiyi sa'ar d'an riqo ba" Abinda ta fadi kenan qasan zuciyarta tana jin kamar a tsakaninsu annin ta fita daban. Anya ba halinsa Allah ya duba ba ya hadashi da uwa daidai da halinsa?. Zaren tunaninta ya katse sanda anni ke magana "Yana da kirki.....yana karamci,yana da tausayi yana da tausasawa amma fa.......ga mutumin daya fahimceshi. Bashi da sauqi ya fiya tsauri,bashi da tausayi ga wanda bai fahimci shi waye ba,bayason qarya.....bayason saba alqawari,bayason yaudara baya son ha'inci......sannan uwa uba baya daukar raini. Abu na gaba muddin zakayi wasa da addini taku ba zata taba zuwa daya ba.....muddin ba zaka kasance karimi kamar yadda yake ba ba zasu taba daina sabani ba,wadannan sune kadan daga halayensa.......ameenatu" Ta kirata da sunanta na ainihi,abinda ya motsa zuciyar sabreen kenan sosai "Ban gaya miki duka halayensa ba don na tursasaki kula da yarona.....na gaya miki ne don na sauqaqa miki qofofin zama dashi....na gaya miki ne don kiyi hanzarin mamaye zuciyarsa......na kuma gaya miki ne don na rage miki wahalar fuskantarsa......naso ace na samu zama da wasu mutane mafi kusanci dake don na tambayi naki halayyar na isar masa dasu a shimfide.....domin cikar mafarkina shine......gidan muhammadu yafi gidan dukkanin wani magidance zama aljannar DUNIYA......gidansa ya zame masa kaffara akan kowanne abu daya fuskanta a rayuwarsa a baya" Anni ta qarashe maganar har tsakiyar zuciyarta tana fatan mafarkinta ya tabbata. Miqa hannu tayi a nutse ta kamo hannun sabreen ta sanya cikin nata "Idan har zaki bashi dukkanin kulawa......idan har xaki nuna masa zallar soyayya irin soyayyar da uwar kewa danta.....idan har zaki kasance me addini tsafta da kwalliya.....xaki kula da abincin muhammadu tabbas kin gama samunsa a tafin hannunki......yana cikin yunwar soyayya da kulawa.....muddin ya samu isashiya da zata qosar dashi babu ko haufi kin gama mallakar zuciyarsa dama rayuwarsa gaba daya". Ta saurara ta kuma fahimci duka zantukan annin,saidai cikin nata zuciyar wani magana takeyi na daban "Inama ace zaki fahimci waye danki sani na zahiri ba fuska biyunsa ba......inama wata daban kike budewa sirrikansa wadda ta shirya xama dashi ba SABREEN me zaman wucin gadi ba". Dole ta sanyashi kashe duka wayoyinsa tun a hanya a sanda abdussabur yake tuqashi zuwa gidan anni. A cikin jikinsa da zuciyarsa yakejin wata irin galabaita da bai taba jin irinta ba saboda zurfafa da tunanin da yayi. Yana da kyau yaci gaba da tafiya a gabar da yake na sanya idanu akan kowanne motsi da abinda dukka yake da alaqa da maamah. A zarginsa me girma da qarfi ya sake hawa kan yarinyar.......ya sake samun gamsuwa da cewa akwai shirin daya shigo da ita gidan,tunda har qarfin alaqarsu yakai girman da zata kebanceta da wata number wayar ta daban wadda shi kansa baisan da ita ba. Wunin yau gaba daya fiye da rabin tunaninsa yau duka ya tafi ne akan hakan. Bazaice maamah maqiyayarsa ce ba.....hakanan bazaice bata sonshi ba,amma ta fifita kudi dukiya da abun duniya sama da tasu soyayyar.......kusan yayi mata fari kuma cikakken sanin da dan adam kan iya yiwa zanen tafin hannunsa koma fuskarsa......bazaiyi wasa da rayuwarsa ba.....hakanan bazai barwa maamah kowacce irin dama ba.....hakanan zai saka yarinyar a wasan da zata qara fahimtar batasan komai ba cikin duniya.....zai dafata da ruwa da kuma jinin jikinta. Yayi sallama ya shiga parlor dinne a sanda anni ke miqa mata wata irin takarda me daukan idanu dake qunshe da littatafai na addu'o'i "Akwai tsaftatattun addu'o'in mallakar miji a ciki,wadanda basu da wani aibu illa ko shirka a ciki,saidai suna matuqar tasiri wajen kama miki zuciyar mijinki a gareki" Ko alamun fa'ida bataji cikin bayanin anni ba......wannan mallkar da take fadi inda zata yiwu ta bawa maamah ita ta mallaki dan nata kamar yadda tace,ita kuma ta sakar mata 'yan uwa tabbas shine zatafi farinciki. Yana zaune yana sauraren anni tana jaddada mata "Ki raqe addu'a da kyau.....a yanzun kece garkuwan mijinki,garkuwar gidanki ma gaba daya" Baki ya tabe yana siririn tsaki qasan ransa. Inda anni tasan wacece ita tabbas da bata wahalar da kanta wajen mata wannan dogon jawabin ba,da tayi saving energy dinta kawai saboda gaba,a sanda zata fahimci wala'alla ko haruffan baqin dake cikin littafin ba zata iya hadawa ba ballantana ta karanta,don shi kam daidai da karatun sallarta bashi da tabbaci akai,don ya sani cewa Allah ya fada cikin qur'ani me girma _haqiqa sallah tana hana alfasha da duk wani nau'in abunqi_. Ya tabbatar da nutsatsiya kuma cikkiyar sallah takeyi bata yadda za'ayi ta kasa rabuwa da dabi'ar karuwanci da bin maza. Ko a motar kamar ba wanda yasan da zaman juna. Kusan nasa tunanin ma na tafiyar dake gabansa ne daga yanzu zuwa kowanne lokaci,yayin da nata tunanin ya.lula duniyar yadda zata fidda 'yan uwanta daga wannan wasan da bata shirya shigarsu ciki ba. Sanda suka isa gidan sam bata wani jira guard sun bude mata qofa ba,gurds din da take mutuwar jin haushinsu tun daga sanda suka hanata rawar gaban hantsi a gidansu. A yanzu kuma a wannan gidan ta fahimci dasu ake kowanne motsi,wannan wacce irin masifa ce kamar raqibu da atidu da buwayin sarki ya saukar maka da suka zama lallai ka rayu dasu don su dauki dukkan ayyukanka,masu kyau ko akasin haka. A gaggauce ta wuce duka falukan ta zarce hallway zuwa bedroom din,burinta kawai ta isa ga gallababbiyar wayar ta hadu da maamah. Da zafin nama ta birkita inda ta aje wayar kafin su fita,saidai kuma sama ko qasa ba wayar ba dalilinta. Cak ta tsaya tana gwama numfashi,sai kawai ta bude jakar data dawo da ita ta fidda asalin wayarta da take kiran kowa da kowa da ita. Asalin layin maamah din ta kira,wanda bugu biyu ta daga,saidai bata jiyo komai ba sai muryar haneefa daga gefe da alama hira take mata ita kuma tana fadin "Allah auta?" Idanu ta runtse,ta lura da gaske ta shiryawa wasan...... Ta ruwan sanyi takeso ta cutar da rayukan da basuji ba basu gani ba. "Me kikeso?,me kike buqata?" Ta tambayeta kai tsaye ba tare data damu ta amsa sallamar data mata ba. Wani shu'umin murmushi ta aje,sannan ta jita tana cewa "Haneefa jeki kwanta kema,idan na gama zanzo na daukeki mu wuce daki tare" "Tom" Ta amsa mata kamar yadda yawanci haka maganarta take,abun kuma daya sake sokar zuciyar sabreen kenan. "Mallakamin d'ana nakeso kiyi.....ni kuma zan mallaka miki 'yan uwanki ta ruwan sanyi,dama naki ne". Tayi mata bayanin hankali kwance. Suya sosai taji zuciyarta tanayi,tanason fadin maganganu da dama......tanason tayi abubuwa da dama amma kaman an danne harshensa sai zallar bacin ran dake mata zullo "Why ni?,me yasa saini ne?" Ta fusgi kalmar daga harshenta ta watsawa maamah ita. "Saboda ni a wajenki kawai na hango irin zarrar da nake buqata......a aikinki na gano abinda zaisa aikina ya cimma gaci.....uwa uba kina da wani irin kyau da zai iya saurin rusunar da zuciya ya kuma narka zuciyar kowanne d'a namiji". Qit kawai ta kashe wayar tana jifa da ita gami da cusa dukka yatsunta goma cikin sumarta. Maganganun maman sun isheta haka,a yanzu basu take da buqatar ji ba. Kowacce tsiga ta jikinta ta miqe,taji wani irin matsuwa da fatan isowar kayan aikin maamah din hannunta. Inama ace zai yuwu ta danneshi tayita dura.masa abincin?,daga safe zuwa yamma ya zame mata mallakakke kaman yadda takeso ita kuma ta samu yancin 'yan uwanta. Tabbas! Inda babu 'yan uwanta da maamah din tayi garkuwa dasu,babu abinda zai hanata nuna mata ainihin kalarta da kuma ainihin yadda wasan zai gudana. *DUNIYATA LITTAFI KUDI NE(PAID BOOK)* 08187255862 𝐃 𝐔 𝐍 𝐈 𝐘 𝐀 𝐓 𝐀 _ZAFAFABIYAR_ ̶B̶O̶O̶K ̶2 ⱧɄ₲Ʉ₥₳ 𝙋𝘼𝙂𝙀 23 23 Har wani nauyi idanunshi ke masa saboda tsohuwar gajiya da sabuwar gajiya dake a jikinsa,ga kuma wadda ke jiransa a gaba. Wanka ya fara yi,sai kawai ya sauya pyjamas dinsa ba tare da yabi takan abinci ba don baijin gajiya zata barshi yayi hakan yabi lafiyar lallausan gadon nashi dake gewaye da kyawawan pillows daa luxury bedsheet din dake qarawa bed din zama wani na musamman me cike da alfarma da wata nutsuwar samun lafiyayyen bacci. Numfashi biyu kacal ya sauke wani lallausan ringtone ya katse masa relaxing din da yayi. Duk kiran da zai shigo wayar yasan na wani makusancinsa ne,hakanan a baya so din ya miqa hannu ya dauko shafaffiyar wayar me wani irin kyan daukan hankali. Sunanta da ya gani ya sanyashi miqewa daga kwanciya zuwa kashingida zuciyarsa tana bugawa,ya lumshe idonsa yana budewa lokaci daya,can qasan ransa yana fatan Allah yasa ba wani jagwal dinne ya taso ba ko zai sameshi. Cikakkiyar sallama yayi mata,ta amsa da wani irin yanayi na karsashi da kulawa. "Akwai baqi a qofar gida,sun gaya min securities na gidan sun hanasu shigowa" Har ya sauke qafafunsa qasan gadon da zummar yaje ya duba ta na'urar tsaronsa,sai ya tuna ashe ba'a gida yake ba nan wani sabon muhalli ne,baida tabbacin an gama installing nasu,dole ya koma ya zauna gefan gadon a nutse yace "Baqi kuma maamah?....at these late hours?" "Eh......ba wasu baqi bane......me aiki ce nace tazo don ta tayata zama,da kuma yanayin gidan naku dole saida mataimaki daban". Numfashi sosai ya zuqa yana fesarwa,kowanne taqi kuma kowanne taku da motsi na maamah magana ce me zaman kanta.....wanzuwar aiki ne da sai ka saka hasashenka da kyau zaka iya cimmasa. "Amma maamah ina tunanin tafiya zamuyi.....dani da itan gaba daya jibi idan Allah ya kaimu....so koda tazo dinma zata zauna a gidan ne ita kadai.....nace if possible ta bari idan mun dawo....i will call you saiki turota" Har tsakiyar kanta taji wani abu ya tsarta mata,hakan kuma ya bayyana har cikin sautinta daya canza nan da nan,abinda ya sake bashi wani haske. "Har zuwa yaushe zaku dawo?". "2to 3days ne.....just bude kamfani kawai zanyi na dawo" Ya bata amsa bawai yana nufin dukkan maganganun daya fada haka suke ba. Duk da bai iya qarya ba......amma a wannan muhallin ya samu fatawar qarya a kansa a yanzu halastacciya ce. Adadin kwanakin da taji basu da yawa sai taji damuwarta taqaitacciya ce........ta cika da fatan tafiyar ta sake basu kusancin da zai damqa mata dukka amanarsa a hannunta,yadda suna dawowa komai zai fara cikin sauqi aminci da kuma nasara "To yayi baida damuwa.....ammmm amma ba....kace su barta ta shigo na bada saqo ta bawa d'iyata". Kai ya jinjina yana cewa "Alright" Sai ya gintse kiran. Wadanda suke on duty ya duba sannan kai tsaye ya kira daya daga cikinsu. Saidai kafin basu damar bata damar shigowa sai daya basu dan qaramin aikin da tun kafin zuwaira ta qarasa ciki suka gama aiwatarwa suka tura masa. Bawai bayan ta shigo cikin gidan ba......tun daga farkon layin daya amsa sunan MUHAMMAD JADDA STREET ta gama raina kanta dama komai nata,bata sake tsinkewa ba sai da suka iso qofar gate gate guda biyu da fuskar gidan ke dashi daban daban......ta gama kuma narkewa gaba daya tun daga harabar gidan har zuwa falon farko da suka zauna suna dakon sabreen. Kowanne motsi da yadda laila ta gaza sukuni,ta kasa danne zallar zalamarta da kuma dimuwa da yadda gidan yake duka kan idanun zuwaira take yinsu,zuwairan da tayi banza da ranta tamkar ma batasan tanayi ba. Mummunar qullaci ta samu zuciyarta dayi akan hajja harira.....ko maamah bata fuskanci manufar harira na hadota da ita ba ta gama karantar komai.....baqinciki qyashi da hassadar ta zauna ita daya a gidan take mata......to itama ta lashi takobin zata gara nata wasan akan laila da hajja,zata kuma murza musu kalar nata zaren. Karo na biyu kiran daya shigo mata yadan darsa mamaki a ranta,saidai a yanzun da 'yan uwanta ke tare da ita,bata jin zata iya tsallakewa kowanne kira da zatayi mata.....don tana cike da tsoro da fargabar shudewar kowanne minti a sanda suke tare da ita. "Ki sauka zuwa falonki kina da baqi.....saqon farko kawai naci su baki.....kiyi qoqarin fara amfani dashi daga gobe zuwa jibi". Bata jira cewarta ba ta katse kiran,saita sauke wayar daga kunnenta tana binta da kallo kamar bata gane yaren da maamah tayi magana dashi ba. 𝐌𝐢𝐧𝐭𝐮𝐧𝐚 𝐭𝐚𝐥𝐚𝐭𝐢𝐧 𝐛𝐚𝐲𝐚 𝐝𝐚 𝐬𝐮𝐤𝐚 𝐬𝐡𝐮𝐝𝐞 Daidai sanda jerin motocinsa ke fita daga gidan don komawa nasu gidan,tana zaune daga gefe zuciyarta tayi wani irin nauyi dauke da tarin kalamai da al'amura da tayo tsarabarsu cikin gidan. Tasan tayi qasa d window din motar sanda amna tayo mata rakiya tana mata bangajiya,amma batasanma bata maidashi ta rufe ba saboda yadda zuciyarta tayi nisa a wani bigire na daban. Daidai lokacin da yake zaune bayan motarsa yana danna wayarsa yana qoqarin neman location na gidan da yazo din. Nishin motocin yaja hankalinsa ya cire kansa daga wayar yana maidawa kansu. Motocin muhammad fuad jadda daban suke,kaman yadda komai daya shafi jadda diamond chore resources ya fita daban. Cikin qirjinsa yake jin buri da fatan inama ya kasance tamkar wannan matashin me matuqar sa'a?.....wanda ya fado duniyarsa da wani irin sa'a da yayi Imani ba kowanne dan adam ke samun koda shigenta ba. A lokaci na quruciya......da qananun shekaru sanda jini ke zagayawa da kyau a jikinsa......ace ya mallaki d'anyun kudade irin wadannan?.....ya mallaki kyau da sura irin wannan?.....yayi wani irin tambari da kuma suna,sunan daya watsu sassan duniya dama kuma ba'a batun tambarar sunansa a qasarsa ta haihuwa. Kamar cikin majigin film.....kamar wulqawar walqiya cikin sararin samaniya ya hangi wani Kyakkyawar fuskar......fuskar daya aza dukkanin burinsa a kanta......fuskar daya sha kwana ya tashi da cikakkiyar sha'awarta tare da tunanin yadda zai maidata ta zama tasa har abada......fuskar da daga qarshe ta jefashi cikin bala'i masifa da barazanar faduwar kowacce daraja arziqi da wadatarsa a yanzu da yaketa fafutukar maidawa......fuskar da a yanzun ba fuskar da yake yunwar nema ya d'aid'aita rayuwarta irinta. Bazai iya cewa ga sanda ya zamo ya kuma diro daga saman motar ba sai da ya fara takawa da zafin nama da zummar ya kamosu,ingarman motocin suka masa wani irin fit suka barshi da kama iska ba tare ma da sunsan meye shirinsa ba. "Damn it!!" Ya fada a kausashe yana kaiwa iska naushi da hannunsa. Da gaske itace matar da muhammad fu'ad ya aura?,da gaske itace amaryar da akace masa ana yiwa walima yanzu haka cikin gidan Alhaji hamza kibiya?. Wani irin shu'umin murmushi ya subuce masa ya mamaye fushin da yake kwance akan fuskarsa,ya koma ya daki bayan motarsa da hannunsa daya dunqule "Good......komai yayi daidai" Ya kuma fada a fili yana buga wani tsalle ya koma saman motar yana ci gaba da sakin murmushi,a hankali a hankali murmushin nasa yake qaruwa kafin daga bisani kuma ya kece da wata iriyar dariya yana sake bugun bayan motar gami da furta "MUHSEENA" ainihin sunan da yake shine STAMP dinshi. Da sauri ya kuma saukowa,ya bude backseat din motarsa ya finciko wata magazine. Magazine ne da suka fidda sanarwar daurin auren da komai da komai,a sama an rubuta da manyan baqin _THE BILLIONAIRE'S WEDDING FATIHA_ Kusan babbban abinda suka yita jaddadawa shine......bikin babban mutum me arziqi kaman muhammad jadda din,yazo ba tare da wasu shagulgula da aka dade ana hasashen za'ayi ba,luxury events da kowa ke mafarkin zaiyi a matakin arziqi irin nasa,shin meye sirrin?. Murmushi ya kuma saki sanda ya karanta tambayar qarshe,sai yaji kaman shi ya cancanci ya amsa tambayar. "How i wish ina wajen da aka buga labarin nan?,tabbas dana basu full details na wacece wadda ya aura,ta yaya zaiyi shagulgula bayan BARAUNIYA ya aura?,TSOHUWAR KILAKI?" Ya fada a bayyane "Ameenatu!" Ya kira sunanta na ainihi dake rubuce jikin katin. "You will pay it......dole zaki biya ninkin farashinki" Ya sake fadi still a bayyane,boyayyen fushin nan dake kwance qasan ransa yana wani tasowa yana bashi tururin bacin rai har saman fuskarsa. A gaggauce ya koma cikin motar tasa ya wurga magazine din,shima ya shige ya kunnata gami da bata wuta ya finciketa yana barin layin don sam yama mance maqasudin abinda ya kawoshi layin. *_S A B R E E N_* Tun bayan sallar asuba take a zaune saman abun sallarta a qoqarinta na hana kanta komawa baccin daya zame mata al'ada duk safiyar duniya. Bata da matsalar shirya su haneefa breakfast da sauransu,duka wannan huda zatayi kafin su wuce,sai yau abun ya zame mata banbarakwai. Zuwa qarfe bakwai idanunta duka sun daddaure mata sunyi mata wani iri,ta miqe a hankali ta ninke abun sallar sannan ta taka tana nufar wata drawer ta zauna gefan gadon tana jawota. Ledar jiya ce da zuwaira ta kawo mata,ta fiddota tana qarewa ledar kallo. Abubuwa biyu suna karakaina cikin ranta,kokwanto da kuma qwarin gwiwa,saidai kuma qwarin gwiwarta a wannan safiyar tamkar yana son korar kokwanton da takeji,don haka ta riqe ledar da kyau ta fara takawa tana fita a dakin. Can qasan zuciyarta ta birkita da tunanin me ya samu wayar momma?,me yasa ta kasa samunta?. Daga daren jiya zuwa asubar yau ta kirayeta har batasan adadi ba,tanaso taji daga bakinta.......tanason taji me yasa tabar su huda a hannun waccar matar?. Tsaiwa tayi cikin kitchen din tana tunanin me dame zata dafa ko ta soya da komai zai narke a ciki ba tare daya bada wata alama ba?. Aqalla ta kusa minti biyar kafin ta wuce store din. *_DUNIYATA LITTAFIN KUDI NE(PAID BOOK),KAI TSAYE KI TUNTUBI WANNAN NUMBER_* 08187255862 𝐃 𝐔 𝐍 𝐈 𝐘 𝐀 𝐓 𝐀 _ZAFAFABIYAR_ ̶B̶O̶O̶K ̶2 ⱧɄ₲Ʉ₥₳ 𝙋𝘼𝙂𝙀 24 24 Inda aka yiwa dankali Kyakkyawar ajiya ta duba,ta debi yadda take ganin zai isa,ta bude freezer shima ta debi nema ta rufe tana dawowa kitchen din. Yau sai gata kace kace cikin hidimar hada breakfast,abinda ya zame mata sai lokaci lokaci idan huda bata da lafiya sannan ta karbeta. Awa biyu ta share cikin kitchen din,sanda ta gama ta gama gajiya gaba daya,amma haka ta zaba warmer ta soma zuba komai a ciki. Sanda ta bude ledar da zummar fara gudanar da aikinta cikin ruwan tea da dankalin data soya da kuma farfesun naman sai taji hannunta yana rawa. Hannuwan nata ta sanya da zummar qulle ledar ta maida ciki amma sai sunan HUDA NADRA HANEEFA ya fado mata......daga bisani maganganun maamah suka dawo.mata fes,sai takejin kamar umarni ne akeyi mata na KI AIWATAR. Kai ta soma girgizawa,'yan uwanta sune haqqin farko da suka zame mata wajibi ta fara kubutarwa.......ba zata wofantar da rayuwarsu ba saboda mas'alar mutumin da ko qanqani baisan zafinta ko darajarta ba,don haka ta kunce komai......takuma aiwatar dashi kamar yadda zuwaira ta zana mata,ta debi kayan abincin ta jerasu saman dining. Tsaiwa tayi tana kallonsu,kamar ba zata bar gurin ba,sai kuma taja da baya ta fara takawa tana sauka daga wajen. ▄A nutse yake saukowa daga saman stairs din,sanye da wata lafiyayyar suit ta kamfanin BRIONI da suka zama number daya wajen fidda suit na manyan mutane daga auduga da zararruka masu daraja. Yayi wani irin kyau sassanyan kyau kaman yadda yanayinsa yake nunawa kamar yau din bai tashi da wannan kuzarin nasa ba dake sake bada bayanin cikakkiyar lafiyar da yake da ita. Qafafunsa sanye cikin rufaffun takalman dake faman daukan idanu suna qara bayyanar darajar da yawan nauyin kudaden da aka sanya aka siyesu. Hannunsa daya cikin aljihun trouser dinsa,daya hannun kuma yana sarrafa wayarsa. Sassanyan turaren nan nasa da bai cika hayaniya da yawa ba ina busawa a hankali yana karade ko ina. Wani irin qamshi ne na musamman dake tashin kan mutane da dama,saidai idan ka debe farouq har yau ba wanda zai iya gaya maka exactly sunan perfume din da yake using. Musaddiq da saddiq sunsha zuwa su sata,amma sun kasa samunshi ako ina bare su siya. A yadda yake saukowa daga shi sai wayarsa zaka rantse ba wata muhimmiyar tafiya bace a gabansa,kamar zaije qofar gidane ya dawo. Haka tsarin tafiyarsa yake,baya daukan komai sai documents dinsa da wasu mihimman abubuwa amma banda sutura. Kusan duk qasa ko garin da yake da huldar kasuwanci dasu yana da permanent gidan da ba abinda gidan ke buqata sai isowarsa.....idan ya sauka a wani gurin daban ba gidajensa ba to yayi hakanne saboda salon bad da hankali da wasa da hankulan abokan adawa na kasuwanci ko kuma dalili na ra'ayin qashin kanshi na haka kawai yaso. Duba daya ya yiwa hallway din ya maida idanunsa ga qofar da zata sadashi da parlor din,sai ya maida wayarsa side pocket na rigarsa sannan ya maida daya hannun shima cikin trouser dinsa yana takawa a nutse cikin falon. Sai daya zagaya falon tas ya gama duba komai,ya tabbatar komai yana a muhallin daya kamata ya zauna,sannan ya zarce falo.na biyu ya tabbatar da komai a yadda yakeson ya zama,sannan ya zarce kitchen zuwa store ya duba komai. Sanda yake baro kitchen din hankalinsa yakai kan dining din dake jere da warmers,ya zubawa gurin idanu na wasu mintuna yana qanqance ido,kafin kuma ya sauya akalarsa yana nufar wajen zuciyarsa cike fal da mamaki. Cak ya tsaya kan warmers din yana sake binsu da kallo tamkar wanda ke neman sunan wanda ya qera warmers din a jikinsu. Ya kusa mintuna biyu kafin ya zare hannuwansa daga aljihun ya fiddosu,bakinsa da yake motsi kadan kadan zaka kalla kasan akwai abinda yake fadi wanda duka bazai wuce addu'a ba,sannan ya miqa hannunsa a nutse zuwa ga warmer din yana furta "Bismillah" A fili,ya murzata ya bude. Daya bayan daya ya bude komai,hatta da hot water dispenser din da tayi using ta adana tea din sai daya saka cup ya zuba ya jerasu a gabansa yana qare musu wani irin kallo na qurilla. Ya kusa mintuna biyar a haka,sai ya saki wani siririn murmushi yana girgiza kai,ya saka hannunsa ya maida komai yadda yake kamar ba'a taba ba. Hannunsa ya miqa daga gefan table din ya ciro sticky notes guda daya,yayi gajeran rubutu ya manne mata jin warmer din ya juya da dan hanzari ba kaman dazu ba yana sauka a wajen. "Tabbas ita din aiken maamah ce......" Abinda ya gayawa kansa kawai kenan ya gangara yana ficewa gaba daya daga falon bayan ya tsinke waya guda daya data rage ta telephone din dake parlor din. Kowanne ma'aikaci yana tsaye a matsayarsa suna jiran dakon fitowarsa. Dukka guards dinsa suna tsaye a inda ya kamata kowa ya tsaya. A yau shigar fari kowannensu yayi,da wani irin tsarin shiga da sutura da zata bayyana alfarmar wanda suke aiki a qarqashinsa. Abdulgafar shugaban tawagar tsaronsa shi ya fara nufoshi a gaggauce cike da kuzari yana tarbarsa cikin girmamawa kaman yadda suka saba shi da mataimakinsa jordan "Good morning sir" Ya fara gaidashi kafin muryoyinsu ya karade wajen suna gaidashi suma "Morning.....hope you are fine?" "Fine sir" Suka hada baki wajen amsawa "Good" Ya maida musu yana gyada kanshi. "Jordan" Fuad yayi kiransa "Sir" Ya amsa yana matsowa. "Where's abdulbasit?" "Am here sir" Wanda aka kira da abdulbasit ya furta yana matsowa cikin shigar wani uniform da yasha banban da nasu jordan "Have you finished?" Kai ya gyada a girmame "Yes sir...." "Okay,kada ka manta.....zan bar muku jordan.....jordan,ba shiga ba fita har sai na dawo ko na bada umarnin hakan. Ko waye bazai shiga ba,ko waye kuma bazai fita ba......hope i made it clear?" "Yes sir" Jordan din ya gyada kai,don shi ya fahimci inda aikin yasa gaba,zasu maimaita salon aikin da sukayi satittikan da suka wuce kenan. "Yi mana addu'a" Ya fada a taqaice yana duban abdulra'uf wanda kusan duk sanda qaramin meeting irin haka ya kamasu shike da alhakin hakan. Cikin mintuna uku aka kammala kowa ya wuce motarsu,motocin suka jeru kamar kullum,security din dake kula da qofa ya wangale musu ita suka fice daya bayan daya. "Am on the way......banason jira" Abinda ya gayawa saddiq kenan da yayi kiransa sanda suke a cikin motar,sai ya kashe wayar kawai ya maida aljihu. Titi ya zubawa ido yana fesar da iska daga bakinsa. Baya tunanin maamah zata saka a kasheshi saidai wani abu na daban,amma ita kuma fa?,may be ta tsallake gona da iri,wala'alla ta wice limit da iyakokinta,amma duka ita maamah bata gani ba?,why zata zabi mace me irin wadannan dabi'u da halayen ta kasance a tare dashi?. Tambayar da yaji ta sake quntata zuciyarsa,abinda kuma bayaso ya faru kenan don yau din yana buqatar freshness don gobe rana ce me muhimmanci a wajensa. *_DUNIYATA LITTAFIN KUDI NE(PAID BOOK),KAI TSAYE KI TUNTUBI WANNAN NUMBER_* 08187255862 𝐃 𝐔 𝐍 𝐈 𝐘 𝐀 𝐓 𝐀 _ZAFAFABIYAR_ ̶B̶O̶O̶K ̶2 ⱧɄ₲Ʉ₥₳ 𝙋𝘼𝙂𝙀 25 25 "Nayi zaton tare zaku tafi?" Shine abinda anni tace dashi sanda yake zaune sosai gaban abba suna breakfast dashi. Kai ya girgiza "Ba daman hakan anni,idan munje ma zata dinga wuni ita daya ne saboda ba zama zanyi ba......akwai baqi da sauran shirin da zamuyi daga yau zuwa goben in sha Allah" Kai ya jinjina "To Allah yayi jagora.....yasa a bude a sa'a" "Allahumma ameen" Suka kusa hada baki wajen amsawa shi da abban. "Amma ba za'a kai mata abokin zama ba?" . Anni ta fada cikin salon nuna kulawa. Basarwa yayi don baison anni ta gane komai game da lamarin "Ba ita daya bace anni,banajin zata damu,akwai mutane a gidan". Kai ta gyada "To Allah ya tsare" "Ameen ya rahman" Ya sake amsa mata. Duka duka mintuna arba'in suka qara suka fice a gidan shi da musaddiq zuwa airport inda private jet dinsa ke jiran isowarsu. A hankali hasken ranar dake ratsowa ta tsakanin labule ya soma qarawa dakin haske yana kuma tabbatar da bayyanar rana sosai ya wuce kai tsaye ya taddata har inda take kwance,wanda wannan shine abinda ya sanya idanunta budewa a hankali suka kuma sauka kai tsaye kan agogon dake manne a dakin. Sha biyu na rana saura minti biyar kacal shine abinda idanunta suka gani,abinda ya sanyata ware idanunta gaba daya tana kuma miqewa da dan sauri. Bayan Hannunta ta saka ta mutstsike idonta tana sake duban lokaci,sam batasan tayi bacci me nauyi haka ba,don ko wanka bata samu tayi ba ta koma ta kwanta bayan ta tabbatar ta gama duk abinda ya dace. Miqewa tayi tana miqa,tana jin yadda gajiya kebin duka sassan jikinta,can cikin zuciyarta kuma tana raya lallai zuwa yanzu ya debi abincin yaci,tana sake jin wani tabbaci da qwarin gwiwar komawarta zuwa ga rayuwarsu ita da 'yan uwanta. Toilet ta wuce tayi wanka,ta fito ta shirya cikin doguwar rigar atamfarJulius gold data zauna mata daidai jikinta da wani irin dinki da bazai takuraka ba. Sai a sannan taji cikinta yana wani yamutsawa....a lokacin ta tuna lokacin data dauka rabonta da wani abu me suna abinci cikakke. Plate tummy dinta ta shafa,sai ta miqe a nutse tana nufar hanyar fita daga dakin. Tun daga nesa idanunta nakan stairs din har tazo ta gotata tana fita falon farkon. Tadan shaqi iskar dake kadawa tsakanin hallway stairs din da parlor din,wani qamshi ne ke kai kawo na daban wanda bata taba jin sassanyan qamshi irinsa ba,wani sashe daban na zuciyarta kuma tana jin kamar ta taba ji ko sanin irin qamshin. Xarcewa falo na biyu tayi,tunda kuma ta fito idanunta suna kan dining din. Gudun zuciyarta ya qaru kadan,yayin da ta cika da fatan taras da komai ya tafi daidai. Bude komai tayi,daga kallon farko ta fahimci ba'a taba komai ba.....daga nan din kuma dukka gwiwoyinta na qafa da hannu sukayi wani irin sanyi,sai taji ta kasa tsaiwa,taja kujera daya ta zauna tana girgiza dispensers din taji ko yawan adadin tea din ya ragu?. Nan ma ba abinda ya sauya,yadda ta zubashi haka nauyin yake,sai ta saka hannuwanta guda biyu tana dafe kanta,daidai sanda idanunta suka sauka kan sticky notes din dake maqale a wajen iska tana dan kadata. Hannu daya ta saka ta ballota daga inda take liqen,ta sanya idanunta akan kwantaccen rubutun dake a tsare kamar wanda aka tafa a inji bawai hannune yayishi ba _mission accomplished_ iya abinda takardar ta qunsa kenan. Jujjuyata ta shiga yi tanason fahimtar saqon dake rubuce a jiki amma ta gaza kaiwa ga nan,abu daya ne kawai ya tsaye mata a rai da baici din ba. A niyyarta ta koma daki ta zauna ta jira wai koda zai sauko yaci bisa rashin sanin ya dade dayin nisa cikin gajimare. Amma qaguwa dason taga yaci din ya hanata komawar,sai tayi zaune a parlor parlor din tana saka kunne akan kowanne motsi na gidan,amma sam motsin da take iya ji din ba wani motsi bane na azo a gani,don hatta da securities na gidan bawai suna kusa da ita bane bare ta jiyo motsin nasu da kyau. Sha biyu daya daya da rabi biyu biyu da rabi ba wani batun motsin kowa da komai cikin gidan,zuwa lokacin ta fara sarewa da lallai bazaya sauko ba,don koda wasa bata kawo cewa wai baya cikin gidan ba. Koda zai sauko a yadda suka lissafa mata halinsa tayi imanin bazaici komai na daga breakfast din ba,wannan ya sanyata cikin mutuwar jiki ta tattare kwanukan tayi kitchen dasu ta ajjiye tana tunanin yadda zatayi da kayan abincin. A makare ranar tayi sallar azahar......har ta idar da sallar tunaninta ya karkata ga me ya kamata tayi?,ta shaidawa maamah din ko ta barta?,kada sanar mata ya sanyata ta dauka cewa gazawa ce har ta nemi yin wani motsi akan qannenta. Wannan tunanin ya sanyata ta share,duk kuwa da cewa wani sashe na zuciyarta a matse yake data gaya matan,amma ta danne da wani irin qarfin hali tana saka ran zai fito yaci na dare. Tana idar da sallar la'asar ta fada kitchen,ko a sannan ma tsaiwa tayi tana tunanin wanne irin kalar abinci zatayi da zaija ra'ayinsa har haqarta ya cimma ruwa?. Sai data kusa qure tunaninta kaf sannan ta zabi abu daya,ya wuce zuwa store tana duba dukkanin abinda take da buqata. Dab da magariba ta baro gaban dining din data cika da warmers masu dauke da abinci. Tana takawa zuwa hallway din tana satar kallon stairs din. Zuciyarta cike da mamakin wanne irin mutum ne shi haka?,wanne irin mugun baqin hali ne dashi da har zai debi wadannan wannin a qunshe a sama ba tare daya sauko ko anji motsinsa ba? "Ko yana zuwa masallacin ma oho" Ta furta a ranta a sarari tana jan tsaki gami da tabe baki,ta tura qofar dakinta ta shiga tana addu'a yadda a daren nan data saka hope me yawa,ta zuba komai da yawan adadi.....Allah yasa a wannan daren komai ya ratsahi har fiye da yadda maamah din keso don ta samu tickets din matsawa daga rayuwarsu ita da 'yan uwanta. Cikin toilet dinta tayi wanka,takuma shirya cikin sassaqan cotton lite material me sauqi. Sallar magariba tayi,sai taci gaba da zama a nan. A hankali yaran suka fado mata,sai taji tana kewarsu,tana so taji!muryarsu koda kuwa maamah din zata kafa mata wani sharadi na daban kafin ta barta ta gansu,wannan tunanin ya sanyata miqewa a nutse tana mamakin duka yau bata dauki wayarta bata kuma yi amfani da ita ba. Kai tsaye tasan inda ta aje wayar tata,can ta nufa,ta daga wajen da zummar dauka,saidai kuma wayar tace daukeni inda kika ajiyeni. Mamaki kadan ya kamata,amma sai ta share tana tunanin qila ta canza mata waje ne ta kuma manta inda ta ajjiyeta,don haka ta fara bincikawa guraren dake daura da nan ko a nan ta ajiye din. Guri hudu duka bataga wayar ba ba alamarta,ganin zata gajiyar da kanta saita ajiye wannan ta koma laluben wayarta ta asali data barta a handbag din da suka dawo da ita jiya dake ajiye saman mudubin nata tunda ta ajiye jakar. Kaf ta lalube jakar sannan ta zazzageta,saidai babu wayarta babu alamarta a ciki. Mamaki yadan sanyata ja da baya,nan ma zuciyarta ta soma ayyana mata wataqila itama ya canza mata waje ne,don haka sai ta fara jaye jayen lockers tana bincike dakin. Wasa wasa har closet dinta ta duba babu wasu alama na akwai wayoyin. A hankali ta dawo tana zamewa ta zauna daga qasan carpet din da aka qawata gaban sofa bed din tana maida numfashi. "Ya akayi haka?,me yake faruwa?,dukka wayoyinta babu ko guda daya?" Ji tayi sam ta kasa aminta ko ta samu nutsuwa,sai kawai ta fadada bincikenta har zuwa kitchen dining area waiko ta barsu a can,saidai babu komai kamar dai yadda ta gani a dakin. A parlor din ta zame ta zauna,tana jin wani shakka da kokwanto na shigarta. Kota wacce fuska bataga waje ko wani sarari da wani zai samu daman shigowa gida irin wannan ba.....me wasu irin madaukakan katangu da kuma gwabza gwabzan security irin wadannan ballantana tayi tunanin wani ya hauro ya shigo musu...... Da sauri ta zauna sosai tana qanqance idanunta sanda wani tunani ya fado mata. "Idan har haka ne shine kenan ya dauke wayoyin?,yaushe?,garin yaya?,a ina kuma ya samu damar aiwatar da hakan?" Tambayoyin dake danqare a kanta kenan data dinga juyasu. Idanunta ta maida tana duban sashen da stairs dinsa suke,zuciyarta na bugawa kadan kadan,tana jin kamar ta tashi ta haura ta sameshi a can,taji meye hujjarsa na daukar mata wayoyi,bayan hakan ba huruminta bane?. Bata fahimci cewa gidan ba kowa ba......ita daya ke rayuwa a cikinsa duk girmansa ba sai da sha daya na dare ta gota a idanunta. Sai a sannan taji wani irin tsoro ya soma mamayarta sanda zuciyarta ke bata hasashen ita daya ce qwallin qwal a gidan. Wani irin karyewa zuciyarta tayi,tsoro yana sake shigarta sanda take qudundune cikin duvet dinta. Bata taba kwana ita daya ba koda cikin dakinsu ballantana a gidansu gaba daya ba.....wanne irin azzalumi ne shi da zaya fita yabarta a gidan da yafi qarfin zaman mutum hudu ma yace ta kwana ta rayu ita kadai?.....ba wayar da zata kira wani ballanta taji sassauci......koda ta duba wayar girke dake parlor din da zummar ta sadata da security din da suke waje taji ko zata samu aron waya daga hannunsu cikin rashin sa'a ta samu an yanke sadarwarta,ba zata iya yin magana da kowa ba banda dakunan dake cikin gidan. Kanta ta cusa cikin pillow din tana jin yadda bugun zuciyarta ya qara tsananta sanda karen dake wani sashe daban na gidan ya tsananta haushinsa. Bata taba tunanin akwai halittar tsoro a qirjinta har haka ba sai yau.....ashe dukka jarumtar da take zaton tana da ita ba jarumta bace.....ko tace ta tsaya ne kadai ta bangaren saita maza daukan darasin rayuwa da sanin ciwon rasa wani abu da xukata suke tsananin so da qauna. Batasan ya akayi ba ta samu da qyar wani takurarren bacci yayi awon gaba da ita. *_DUNIYATA LITTAFIN KUDI NE(PAID BOOK),KAI TSAYE KI TUNTUBI WANNAN NUMBER_* 08187255862 𝐃 𝐔 𝐍 𝐈 𝐘 𝐀 𝐓 𝐀 _ZAFAFABIYAR_ ̶B̶O̶O̶K ̶2 ⱧɄ₲Ʉ₥₳ 𝙋𝘼𝙂𝙀 26 26 Kwana daya kwana biyu haka awanni suka dinga juyawa da ita cikin gidan,cikin wani irin matsanancin shuru kewa da kuma kadaici. A hankali ta dinga jin wani matsanancin takura,ta yaya zata zauna irin haka ba waya ba gilmawar kowanne dan adam?,tv kuwa sam taqi ta kalleta bare ta gwada kunnata. Da farko ta dauka zata iya jurewa,amma sannu a hankali saita fahimci ashe mutum rahama ne a kusa da kai,koda kuwa ba wata mu'amala da zata hadaka dashi. Tayi dukka juriyar da zata iyayi sai taji haqurinta ya soma gazawa. Wani danqararren bacin rai ne yake cinta game dashi wanda qilan inda yabar mata wayar ma a wannan karon batajin akwai abinda zai mata shamaki daga kiransa ta zazzage masa abinda yake cikinta. Ta yaya ita din da ta kwashi shekara aqalla biyar zuwa shida,ba wata ranar banza da zata fito ta fadi bata fita ba.....yanzu kawai rana tsaka ta wayi gari da mummunan kulle irin wannan?. Ko a baya batata ji a ranta akwai wani lokaci da zayazo a sanyawa qafafunta irin wannan sasarin ba,ba lissafin aure kwata kwata cikin kanta shi ya sanya bata kawo yiwuwar afkuwar hakan a kanta ba koda sau daya. Ranar data cika kwana na hudu,tun qarfe goma na safe taji takai maqurar da ba zata iya jurewa ba. Sha daya da rabi daidai ta kammala shirinta cikin atamfa. Ta taka a hankali zuwa inda take da tabbacin ta ajiye kudinta data shigo dasu cikin gidan,ta bude locker din ta zura hannunta don debosu,don ta gama tsarawa kanta zata taka ta fita ta samu napep duk kuwa da cewa tasan area din kwata kwata yana da wahala kaga abun hawa na haya.....to amma ta gwammace tayi tattaki zuwa babban titinsu tayita jira cikin rana har ta samu abun hawan da zai kaita gida. Zuciyarta da tunaninta gaba daya yana kan taje ta binciki lafiyarsu huda.....kowanne dare dasu take kwana dasu kuma take tashi,suna cikin aminci ko kuwa aah?......da qyar ta iya jure wadannan kwanakin suka shude ba tare da tasan komai game dasu ba. Ta dauka yadda ta dokanta ta fita ne idanunta suke mata gizo sanda ta hangi babu ko burbushin kudi a wajen,amma data bude sosai sai taga gaskiya take gani.......ba komai a ciki kamar yadda ta gani da farko. Mamakinta ya ninku akan mamakinta na kwanaki hudun da suka shude........ta sulale tana sake zama a saman stool din dake kusa da ita. "Wai wa yake da alhakin aikata haka?" Ta sake tambayar kanta tana jin tantama akan tabbacin zargin farko da zuciyarta ta bata. Duk wani karsashi na fitar saita rasashi......yaushe ya samu damar shigar mata daki?,dame dame ya bincika mata?,me zaiyi da wayarta?,dame dame zai bibiya cikin wayar?. Wadannan tunanin su suka sakata a gaba,ta kasa tuna komai ko abinda ya dace tayi,har sai da agogo ya alamta mata sha biyu dai dai na rana. Cikin qarfafawa kai gwiwa ta koma toilet ta sake wanke fuskarta,ta dawo ta wuce closet ta dauki handbag da shoe da zai dace da shigarta sannan ta soma barin dakin tana jefa atm dinta a jaka da zummar idan ta fita ta samu wani guri ta cire kudi daga account dinta. Wannan ce ranar farko kuma karan farko data fito daga cikin gidan a yanayi irin wannan. Faffadar haraba yalwatacciya me wani irin tsari me jan hankali. Kusan gurare da yawa an qawatashi da koriyar ciyawa a maimakon tiles marbles ko concrete da akafi yawan amfani dashi. Sai wasu irin fararen stone da aka zuba a wasu daga cikin hanyoyin da zaka taka ka wuce zuwa haraba ta biyu. Idanunta suna iya gane nata wasu qofofi da babu qofa a jikinsu face wani irin design da aka musu wanda batasan ainihin inda zasu sadaka dashi ba. Sosai harabar ta qawatar da wani irin yanayi da zakayi tsammanin ba cikin qasata nigeria kake ba.....saidai wutar dake can qasan zuciyarta ta danne burgewar da wajen yayi mata,taci gaba da tafiya cikin confidence zuwa qofar gate din da take da tabbacin zata sadata da waje. Tsaye kawai tayi don bata fahimci ta inda zata ratsa ta wuce ba,sam qofar ba irin qofofin data saba gani bane. Gajiya tayi da tsaiwar ta kuma gaji da kallonta da tunanin ta inda zata fita din,don haka ta saka hannu ta soma knocking da tunanin zasu iya jinta. Tun tana knocking din a hankali har ta fahimci ba kowa ke jinta ba,ta qara dada qarfinsa saidai a banza don ba wani motsi da taji da zai bara hope din wani na kusa zaiji ya kuma budeta,wannan ya qara hasala mata zuciya,ko a kurkuku take bangaren muggan laifin kisa ko fashi da makami iya horon da za'ayi mata kenan,don haka ta sake maida kai wajen buga qofar da kyau ba tare da tunanin cewa babu me jinta ba. A hankali wani sashe kadan daga saman qofar ya zuge kanshi da kanshi. Fuskar jordan ta bayyana wannan karon sanye cikin uniform din daya zama kayan sawa ga duk wani ne aikin tsaro dake cikin gidan. "Good afternoon maa". Ya furta da wannan matsananciyar girmamawar da yake mata wadda ba abinda take sawa zuciyarta sai wani irin qarin takaicinsa. Fuskar jordan fuskace da ba zata manta da ita ba ko kadan "Open the door" Ta fada adan fusace tana kallonsa,tana jin kamar ta miqa hannu ta zabga masa mari. Cikin rusunawa da girmamawa kaman yadda ya saba ya fara mata magana da hausa "Am sorry maa......boss bai bada umarni ba,idan ba damuwa ko zaki kirashi kuyi magana tukunna?". Idanunta ta janye kawai daga kan jordan din bacin ranta yana ninkuwa,abinda yayi mata a wancan lokacin shi ya maimaita mata kenan?,waishin me yake daukan kansa ne shi?,don yana da kudi?,yana da dukiya shi yasa yake tunanin zaiyi duk abinda yaga dama?,zai taka wanda takeso a duk sanda yaso?,zai wulaqanta mutane sannan kuma ya kwana lafiya?. Ta ina zata nemeshi bayan babu ko waya guda daya a tare da ita?,ta ina zasuyi magana bayan ya yanke sadarwar gidan gaba daya?,koda ma komai yana nan a muhallinsa ta rantse ba zata kirashi ba. "Kawu ne ya jawo miki" Amsar data dawo cikin kanta kenan. Idan ma kira ne shine mutumin daya kamata ace ta kira,har yanzu tana ji a jikinta kan ta inda ake hawa ta nan ake sauka,kawun shine ya bada ita ya kuma saida mutuncinta.......don ta nata bangaren ba'a kan muhammad fu'ad bane farau shallakewa maza masu kudi da kuma hadari......don haka don shi kadai bazai zame mata matsala ba inda anbi karatun yadda ta saba. Har taji kamar ta sare,sai taga idan ta bari hakan ta kasance yasha da ita,don haka ta matsa bakin gate din "Can you barrow me your phone?". Ta tambayeshi tana kallonsa. Jinin jikinsa yasha,yadan kalleta yana kokwanto. Yaya zata rasa waya tana a gida irin wannan?. "Afwan madam.....amma me zakiyi da waya?" Idanunta da suke mata zafi ta lumshe "Zan kira uncle dina ne.....i lost my phone". Dan jim yayi kadan,sai kuma ya amsa mata yana sanya hannu a aljihu ya fiddo wayar ya miqa mata bayan ya sake bude glass din ya qara girma. Yadda yake bata wayar kamar tana a kurkuku ya sake matsa zuciyarta ya qara yawan adadin bacin ran da take ciki. Wani sashe daban na gidan ta koma ta zauna saman wasu rukunin kujeru da aka qawata cikin wata rumfar bamboo dake bada iska me kyau da sanyi. Da qyar ta iya hada lambobin kawun don ba haddacewa ta taba zama tayi ba.....saidai kawai kira na yau da gobe daya bata daman kallonsu daya bayan daya suka kuma zauna a kanta. Bugu biyu kawun ya daga da cikakkiyar sallamar data kusa sanyata jan tsaki "Kamar gaske" Ta fadi a ranta tana amsa sallamar tasa a daqile. "Wa nake ji kamar sabreena?" Ya fadi da annashuwa cikin muryarsa,zuciyars na bashi tabbacin lallai zama ya soma miqawa,wataqila wani alkhairinma ta bugo tayi masa "Nice" Ta amsashi a hankali "Kai madalla Allah.....ma sha Allah,amma fa naji dadin kiranki kin kyauta diyar albarka,dama inata zube kunne naji kiran naki......" "Eh gashi na kira......na kiraka ne kuma na gaya maka.......wannan mutumin daka saida masa dukka 'yan cina da mutuncina ya kamata ka kirashi ka bashi labarin haihuwata akayi bawai a baiwa aka ribatoni ba.......ka fada masa abinda ke tsakaninka dashi daban da abinda ke tsakanina dashi,bazan iya daukan dukka wannan izzar tasa da izgilancinsa ba......ina da 'yance kafin zuwansa zan kuma ci gaba da kasancewa me 'yanci a rayuwata.....don har yanzu babu d'a namijin da zai dinga ruling dina yadda yaga dama ba tare da naso haka ta kasance ba". "Kai jama'a.....waike wacce irin yarinya ce ne me butulci?,Allah yayi miki wannan babban gamo da katar din da miliyoyin mata ke fatan samu amma ki zauna kina shashanci?,yo Allah na tuba idan ranka ya dade baiyi mulki da izza ba meye zaiyi?,kudi ne dashi fa?,arziqi garai irin arziqin da gwamnati ma wani lokaci biyayya takeyi maka.......ina gani malam rufa'i?,to wallahi bada ni ba.....hasalima ni bamu taba waya dashi ba,dan uwansa kuwa farouqu bazan dauki sirrin gidan ma'aurata nakai masa ba Allah bazai la'anceni ba,in zaki nutsu kiyi biyayya ki tara abinda kika tara karki mana buqulu to,amma wannan jan kunnen bada ni ba.....wane mutum inji mutuwa,Allah baki da hankali sabreena" Har ya qare maganganun idanunta suna kulle saboda yadda yake mata magan da qarfi da hayaniya,uwa uba ita bataga dalilin dogon jawabinsa ba. "Kawu" Ta kirashi a nutse. "Yaushe su huda suka zama cikin kayan gado da har za'ayi rabonsu zuwa ga wata mace da basu hada alaqar komai dasu ba?". "Wata mace?,Allah na yarda dai da gaske akwai sauran qarancin nunar hankali a tare dake.......kina magana akan hajiya mariyah surukarki?,mutuniyar kirki me yawan alkhairi da son zumunci?,yo wannan kika fadi mummunar kalma a kanta aisai Allah ya tsine miki albarka.......ni baza'a zageta dani ba,sai anjima sabreena" Kafin ta ankara ya yanke wayar,abinda ya sanyata a razani ta maida dubanta kan fuskar wayar tana kallonta cikin mamaki. A wannan karon duk yadda taso tare kukan sai da hawaye ya sauko mata bayan ta maida wayar wa Jordan. Sai kawai ta soma tattaki da sassarfa tana komawa ciki cikin yankewar kowanne tsammani. A falo na biyu ta zube don ta gaza isa bedroom din. Wasu irin hawaye masu zafi suka fara gangaro mata. Me yasa rayuwa zata juye mata da zazzafan yanayi irin wannan dare daya?,yanayin da ko s mafarki bata taba tunanin zaya risketa ba?. Ya cika mugu na gaske,ya rufe mata kowacce qofa ko hanya da zata samu sassauci......me ya rage ita kuwa tsakaninta dashi banda itama tayi duk yadda zatayi tayi nesa dashi?,me ya rage banda ta aiwatar da nufin maamah a kansa don ya gwada shiga halin mulkin mallakawa d'an adam yaji idan hakan da dadi?. *_DUNIYATA LITTAFIN KUDI NE(PAID BOOK),KAI TSAYE KI TUNTUBI WANNAN NUMBER_* 08187255862 𝐃 𝐔 𝐍 𝐈 𝐘 𝐀 𝐓 𝐀 _ZAFAFABIYAR_ ̶B̶O̶O̶K ̶2 ⱧɄ₲Ʉ₥₳ 𝙋𝘼𝙂𝙀 27 27 ★★Madaidaiciyar haraba ce wadda yanayinta yayi kama da gine ginen turawa ainun,irin gine ginen qasashen qetare,saidai kuma ba harabar kadai ba.....gidan dama sauran gidajen dake wajen dama unguwar gaba daya ba zaka dauka kana cikin abujar nigeria bane ba. Tamkar shi daya ne cikin gidan saboda rashin hayaniyar jama'a da kuma motsi,saidai a yawancin lokuta yakan zabi yanayi irin wannan don bawa zuciyarsa hutu da kwanyarsa. Bayan doguwar gwagwarmayar tabbatuwar buduwar kamfaninsa ap lagos kwanaki uku da suka wuce,sai ya zabi tsaiwa a abujan don ya sanya ido game da gudanarwar kamfanin koda na sati guda ne kafin ya koma bakin nasa ayyukan da suma a yanzu suke buqatar hankalinsa. Farin boxer ne a jikinsa da wata cotton shirt me gajeran hannu wanda ta bayyana ginuwar muscles na jikinsa,zubi da qirar qarfin da yake da ita. Tataccen natural ruwan blood orange ne a gabansa da ba'a sirka masa shi da sinadarin komai ba kaman yadda yake dabi'arsa ce a haka. Yafison komai natural da za'a sarrafashi da hannu,duk irin dukiyar da yake da ita amma yana sarrafa kanshi wajen sanin abinda zaici,wannan ya sanya yake da wata irin cikakkiyar lafiya. Wayoyin dake gabansa ya sake maida idanunsa akai,ya sake miqa hannu ya dauki daya daga ciki yana jujjuyata. Ba komai a ciki,baiga kuma komai ba. Dayar number maamah dince kawai akai,ba contact ko daya,kaman yadda ba massages a ciki,duk wani social app dake kai baya aiki ba'a budeshi ba,kamar yadda daya wayar take itama. Ba Facebook ba insta ba tiktok,ko watsapp babu duk da yana zaton an taba amfani dashi a kanta an rufe ne. Yanason ya zurfafa binciken sama da haka,amma sai wani sashe na zuciyarsa ya tunasar dashi haramcin zurfafa bincike akan dan adam......amma su ya halatta ya bincikesu har haka?,bayason maamah taci gaba da jefa qafafunta cikin halaka.....dole uwa uwa ce.....mutum daya ce duk duniya ke amsa wannan sunan......kamar yadda yayi imani yarinyar sai ya karanta mata menene rayuwa kafin ya sakar mata qofofin 'yanci ta yadda ba zata sake zama guba ga kowa ba. Maida wayar yayi ya ajiye,yana jin kamar zuwa yanzu ya kamata ya wuce gida hakanan ko don hankalin anni ya kwanta. Ya fahimci kamar tana zargin bai taho da yarinyar ba,amma da yake gwanar kawaici ce ita bata ce masa komai a kai ba. Ya sani ma inda farouq yana nan zuwa yanzu da tuni ya tona mishi asiri,sai Allah yasa suka shiga wata seminar kwata kwata bashi da lokacin kanshi. Wayarsa ya dauko ya lalubi saddiq "Kana ina ne?" Kanshi yadan shafa cikin jin shakka da nauyinsa "Katamfe extension" Ya amsa masa yana addu'an kada ya masa fada. Bayajin doguwar magana a kansa sosai,hasalima wata kasala ke damunsa,ruwan dumi yakeso yasha ya sake kwanciya,don haka kawai ya bashi saqon a dunqule "Kayi magana da team su shirya flight,gobe zamu wuce gida" "Okay in sha Allah" Ya amsashi yana jin dadin yadda bai matsa masa ba bare ya sanyashi baro soyayyar da yake raino a lokacin. Wayar ya mayar aljihun boxer din nasa,sannan ya dauke sauran kayayyakinsa da suke wajen ya fara saukowa daga farfajiyar dake a matsakaicin tsaho,shi ba upstairs ba shi ba qasa ba,amma lallai saiya biyo ta cikin dab da qofar parlor sannan ya shiga parlor din ya wuce duk inda zaije. Sam hankalinsa ba'a wajen yake ba sanda yake saukowar,cikin wani irin mamaki qofar parlor din ta bude sannan ta bayyana gaba dayanta cikin ba zata. Saura kadan ya hada jiki da ita,don ta shigo ne da wani irin zafin nama,banda shima me zafin namar ne yaja baya da sauri da ba abinda zai hana jikkunansu haduwa guri guda. Cikin second biyu ya maido hankalinsa jikinsa,suka fara yiwa juna kallon kallo. Fareeda,d'iya ga ambassador din nigeria a qasar china. Matashiyar da duniya ke gara mata fiye da yadda takeso,ta samu gata.....ta samu ilimi.....ta mallaki kyau......tana da tsananin wayewar da bata barinta fayyace daidai a addininta da ba daidai ba.......wayewar dake haska mata komai ya yiwa ranta dadi.....komai ranta keso daidai ne,wayewar da gatan da sukayi mata jagora tare da nuna mata kome takeso lallai zata sameshi ta kowacce hanya. Doguwa ce fara sannan kuma siririya,wadda ke tattalin jikinta da amfani da mayuka da kuma supplement masu tsananin aji da tsada ba tare data bari zallar hutun da take ciki ya zama jagoran gyaruwar komai nata ba. Zai wahala ka kalleta ka kirata da mummuna kai tsaye......saidai bata cikin sahun kyawawan da kallo daya zai sanya ka gamsu kyakkyawa ce,tana mataki na kyau a middle class....duk da tana kai kanta high class a koda yaushe tana ganin ta cancanta da aje kanta a can. Ta jima tana jin sunan muhammad fu'ad jadda yana gilmawa kunnuwanta.....wani lokaci daga bakin manyan friends dinta yaran gata irinta,wani lokaci kuma daga bakin mahaifinta. Saidai ko sau daya hakan bai taba jan hankalinta ba,saboda tana da wata izza akan namiji da saidai ya nemeta,don ta hada komai da take ganin babu kalar d'a namijin da bata zarce masa ba......in fact tana tunanin ma ita har yanzu cikin wannan duniyar da muke ciki babu kalar mijinta. Sau tari idan sunan ya gilma mata kawai tana surantashi kamar sauran alhazawan masu kudin dake hauka a kanta,masu shekaru,kai duka furfura ko kuma furfurar ta fara ketowa,masu qiba da ajiyayyen tumbi,masu matan aure uku hudu da tarin 'ya'ya. Bisa rakiyar tilas data yiwa mahaifinta nigeria don zuwa bikin bude company din JADDA SPARKLE WORLD daga nan su qarasa garinsu gaisuwar mutuwar qanin mahaifinsa da ya kusa cimma wata uku da rasuwar amma bai samu zuwa ba. Kafaffe kuma tsayayyen yaya ga kakansu qwaya daya daga rage shi ya zuba bala'i akan fareeda,sam yarinyar ba wanda ta sani a cikin su kaf,saboda rabonta da garin tun batafi shekara biyar ba a duniya,basa qaunar zuwa kwata kwata,wannan ya sanya mahaifinta ambassador khaleed mustapha ya tilasta mata saboda rufe bakin mutane. A karon farko da sanarwar bayyanar me kamfanin kan dandamalin jawabi ta ratsa microphone din,ta daga kanta daga kan wayarta da take qoqarin posting hotunanta a shafukanta,ta kuma saukesu akan muhammad fu'ad dake tsaye gaban abun magana yana daidaitashi yadda zai dace da bakinsa. Wata lafiyayyar suit ce a jikinsa data tsone idon duk mutumin dake zaune a wajen. Suit din da musamman aka sarrafata tun daga qasar Italy saboda rana irin wannan. Ta sake fidda tsahonsa da murjewar jikinsa da wani irin mahaukacin kwarjini da ya zame masa garkuwa wajen karya maqiya da abokan gabarsa. Idanunsan nan masu wani irin kyau da bata taba ganin irinsu ba suna yawo saman fuskokin tarin al'ummar da sukazo wajen saboda shi yayi cikakakkiyar sallamar da duk wanda ya sanshi yasan wata abace da baya tsallakewa yinta ako ina koda wanne irin mutane ne a gabansa,ba ruwansa da banbancin addini qabila ko kuma yare.....ako yaushe yana yin abinda xai ci gaba da tuna masa....zai kuma ci gaba da bayyanawa ko waye suke tare cewa SHI MUSULMI NE. Sanda ya fara jawabin taron da wani irin tataccen turanci da lanqwashewar harshen da zaka rantse cikin fadar queen Elizabeth aka haifeshi sai dataji kowacce gaba ta jikinta ta saki. Wani irin abu da bata taba ji akan kowa ba ya soma bin sassan gudanar jini na jikinta yana aika saqo wa zuciyarta,wanda kafin ya kammala bayanansa ya sauka gaba daya ya wuce da nutsuwarta dama zuciyarta gaba daya. Ta fahimci akwai ire irenta da yawa a wajen bayan tashin taron,saidai ba alamun samun fuska ko dama daga wajen kowacce diya mace,wannan dalilin ya sanya tabi ta hanyar mahaifinta. Ta samu damar gaisawa dashi,saidai abu na farko daya sanyaya mata jiki hannu data bashi da nufin suyi hand shaking kamar yadda yake gaisawa da kowa,sai ya jefa mata wani irin kallo ya maida hankalinsa ga wani abu na daban. Bata haqura ba sai data sanya mahaifinta ya nema ganawa dashi a masaukinsa dake banana island kafin yabar lagos kenan,a nan ta fito kanta tsaye ta gaya masa abinda ke dauke dashi,amma sai ya saki wani murmushi daya qarasa qona mata ruwan jiki gaba daya,ya kuma bata saqon daya kusa tashin kanta a aiki. "Am so sorry kinji....ni bana soyayya.....infact ba time na ire iren wadannan shirmen,ina fata kema zaki maida hankalinki akan karatunki okay?" Gaba daya shirme ya dauki abun,yadda ya tsaya ya mata maganar ma ta tabbatar albarkacin mahaifinta taci. Still bata jin zata iya haqura dashi,ta samu daman ganinsa a karo na biyu ba tare da yasan ita bace. A nan ta gane ainihin wayeshi,ya fiddo mata true color dinsa,abinda ya birkitata kenan,batayi qasa a gwiwa ba ta bashi tabbacin bata taba neman abu ta rasa ba.....a kansa kuma ba zata fara ba,zatayi duk yadda zatayi don ganin ta mallaki soyayyarsa ta kuma mallakeshi.....ta kuma ci masa alwashin duk inda ya shiga tana biye dashi har sai randa ta samu abinda takeso. Ko a yanzun zare rafkeken sunglasses din idanunta tayi tana qoqarin sakar masa murmushi,yayin da ransa ya motsu da zummar baci amma kuma mamaki ya mamaye wannan gurbin. "May i ask who's let you in?" Yayi maganar yana qoqarin danne fushinsa. Murmushi ta kuma saki tana rolling idanunta cikin salon jan hankali "As your guest,i think you should welcome me first" Ta furta tana narke murya. Baya ya sake ja kadan ganin tana qara takowa inda yake "What brings you here?" Wannan karon ya fada adan tsaurare,alamun bacin ransa suna fitowa fili. Kallonsa tayi a kaikaice tana sake yadda da maganganun da aka gaya mata a kansa. He's not a womanizer,he's not into playing games with women......ta yaya kike tunanin zakiyi winning kansa?" . Ta tuna da maganar da daya daga cikin qawayenta suka mata. A lokacin ta dauki zancan nata ne a matsayin kishi,saboda samun cikakakkiyar dama da tayi da take ganin zata kawoshi cikin rayuwarta,damar da mata da yawa suke nema basu samu ba. "Am here for you fu'ad.....please ka bani gurin zama tukunna mu tattauna a nutse" *_DUNIYATA LITTAFIN KUDI NE(PAID BOOK),KAI TSAYE KI TUNTUBI WANNAN NUMBER_* 08187255862 𝐃 𝐔 𝐍 𝐈 𝐘 𝐀 𝐓 𝐀 _ZAFAFABIYAR_ ̶B̶O̶O̶K ̶2 ⱧɄ₲Ʉ₥₳ 𝙋𝘼𝙂𝙀 28 28 "Get out of my house" Ya fadi ba alamun fara'a ko walwala a tattare dashi. Wannan fuskar me cike da miskilanci,wadda zai wahala kaga wani abu me kama da murmushi a kanta ta sake dinkewa tsaf "Please mana" Ta fada da wata irin shagwaba tana hade hannayenta waje daya "Zaki fita ko sai na kira masu fiddamin dake?" Ya kuma fada yana ware mata idanunsa da suke da wani irin kyau me jan hankali wanda suka sake fusgar hankalinta. Bai ankara ba bai kuma taba kawo haka zata kasance ba ya tsinceta ta fada cikin faffadan qirjinsa tana neman kai masa kyakkyawar runguma. Baiyi wata wata ba bai kuma sake bata koda minti biyar a jikinsa ya yakiceta ya watsar gefe. Wani irin tafasa zuciyarsa keyi,wanna shine karo na farko da wata mace ta rungumeshi irin haka. "Tashi ki fita thn ranki bai qarasa baci ba,stupid!" Ya fadi a tsawace yana nuna mata qofa. Miqewa tayi tana kade jikinta,duk da ba wani baci tayi ko datti ba saboda gurin fes yake da wata irin tsafta da take ta'ammali da ita a komai nasa,cikin borin kunya tace "Yakice ni daga jikinka baya nufin fidda soyayyarka daga zuciyata......zan tafi,amma kuma zan dawo,zan kuma ci gaba da kasancewa dakai,zan zama cikin kowanne motsi naka har sai na cimma nasara na samu abinda nakeso". Daga wannan ta dauki jakarta tana nufar qofa da dan sauri,qasan zuciyarta da tsoron yadda mode dinsa ya koma,amma abinda takeji a kansa ya danne komai. Iska me zafi ya furzar yana shafa sumarsa da tafin hannunsa. Kwata kwata yaqi jinin mace maras jan aji........yana matuqar son mace me aji.....mace me dan wani tasiri kadan na girman kai,wanda girman kai a wajen mace yana alamta alamu na kamun kai,girman kai yana cikin siffar da akeson mace dashi.....amma a mu'amalarta da maza kamar haka. Komawa yayi saman kujera ya zauna yana fidda numfashi me huci. Yana daya daga cikin abinda yasa ya rasa interest akan mata,yana daya daga cikin abinda ya sanya har yanzu ya kasa gano macen da zata sace zuciyarsa kwata kwata.......saboda yanzun mata yana hangen sun rasa dabi'un nan guda biyu zuwa uku masu tsananin tsada fiye da diamond...... Masu tsananin zame musu ado fiye da adon gold a jikinsu,wato KUNYA da kuma KAMUN KAI. Wayarsa ya dauka ya kira abdus_samad yana qoqarin danne fushinsa,bugu daya tak ya daga "Who gave her permission to enter?" Tambayar da yayi kenan a taqaice. "Am sir......" Ya fada adan daburce don jikinsa yana bashi laifi yayi "Did someone invite her in?" Tambayar ta qarasa daburtashi gaba daya,ya kuma fahimci laifi yayi. "Am sorry sir......am sorry,naga diyan ambassador....." "Keep quite......are you out of your sense?,don diyar ambassador ce?,meye alaqana da ita?,dama akwai wannan tsarin na ku barmin mutane suna shigomin guri anyhow?,meye amfaninku idan haka zata ci gaba da kasancewa?" Ya kasa magana kawai sai haquri da yake faman jera bashi,don tunda yake dashi irin fada irin haka bai taba hadasu dashi ba. Bai jira cewarsa ba ya yanke wayar yana ajiye wani tsaki. Ji yayi sam zaman parlor din ya isheshi,bama parlor din bama,abujan gaba daya,ya miqe yana wucewa bedroom dinsa,cikin jikinsa gaba daya yana jin kamar ya yanke inda nata jikin ya tabashi. Bacin rai sosai yakeji a qirjinsa,duk wani nau'i na sabo ya tsaneshi,sai yau gashi ta sakashi abinda yake matuqar gudu da kaucewa. Yasha shiga harkoki da abubuwan dake cakude da mata,amma yanayin kamewarsa da kuma miskilancinsa yasa suke tsoronsa matuqa,ba wadda take zuwa masa da zancan banza,tun daga secondary school university da tafiyansa service,duka Allah ya tsareshi ya kuma tsare imaninsa,duk da irin farkamakin da yake samu. Yana gaban wardrobe yana sauya kayan jikinsa yaji ana masa knocking,muryarsa can qasa da sauran tasirin bacin rai a ciki ya tambaya "Waye?" "Saddiq ne hamma". "Come in" Ya bashi dama lokacin da yake sanya rigar jikinsa. Yanayin yadda yaji sadiq din ya shigo ya tilasta juyawa yana duban fuskarsa. Sai yabi hannunsa da kallo wanda yake dauke da system "What's wrong with you?" Ya tambayeshi yana tsareshi da idanu. Kasa amsa masa yayi,sai daya samu waje ya zauna daga saman carpet ya ajjiye system din sannan yace "We got the announcement........ana zargin an samu muggan qwayoyi cikin jewelry company dinmu". Ya qarasa fada yana buda masa saqonnin da suka samu daga dukkan kafofin dake da alaqa dasu daya nabin daya. Hannuwansa kawai ya zube cikin aljihunsa yana kallon system din. Yanajin wani yanayi yana zagayashi,hankalinsa nason tashi amma yana gayawa kansa da kansa "All is well" A irin wannan lokutan na tsanani,lokutan da jarabawa irin wannan ke tunkararsa rauni yakan rugo da gudu ya mamayeshi.....a irin wannan lokacin yakanji yana da buqatar wata halittar a gefe da zata same masa qwarin gwiwa......banda qannensa banda farouq da yawan daukan mas'alolinsa yake ganin suna masa yawa,ya kamata ya rage masa daukan matsalolinsa haka.....tun daga quruciya kunnuwan farouq zuciyarsa dama gangar jikinsa suke fama da matsalolinsa.....zuwa yanzu ya kamata ace ya huta.....anni,wata irin rumfa ce sha shirgi ita da abban gaba daya,ya kamata kunnuwansu su samu sassaucin jin damuwoyinsu a yanzu haka da girma yazowa kowannensu.......akwai personal mutum da yake buqata daga gefe da zai zauna a wannan matsayin. "Hamma wannan saqonnin barazanar basa da alaqa da faruwar wannan abun kuwa?". Kai yake jinjinawa sanda yake takawa a hankali yana matsawa daga wajen "Definitely......but I'll make it clear im not Intimidated" Ya fada da wani irin qwarin gwiwa yana dora top saman rigar t.shirt din jikinsa. "Let's go.....ka kira William kace ya samemu a can....." "Amma hamma.....flight isn't ready" "We'll take the road" Ya furta yana riga saddiq yin gaba. Kafin sukai ga isa lagos ya gama shirya dukkan abinda ya kamata ace ya tsara din. Suna dab da shiga garin har a sannan idanunshi biyu,ko daya baiji wani buqatar bacci ko kuma ya huta ba. Yaja qaramin tsaki sanda suka dauki hanyar kamfanonin. Ya fahimci ita kalmar SO ko a meye ta shiga wahala ce kawai da walagigi da ruhi,wannan ya sanya banda soyayyar family dinsa bai taba saka soyayyar komai cikin ranshi ba,sai yanzu gashi kwatsam......kamfanin ya shiga ransa har baisan adadi ba......gashi kuma ya zama abu na farko da son nasa keson zame masa wahala,da wannan ya qara ji a zuciyarsa lallai tabbas ya kamata ya nisanci soyayya iyakar iyawarsa. Duk da sun nuna matsayinsa yafi ya taso da kansa amma ya kauda wannan. Ya karbi duk wani bincike nasu ya dora da nashi. Da gaske an samu wani dan qaramin store cikin kamfaninsa cike da qwayoyin da inda wani me qaramin matsayinne ba shakka sai ya tafi dauri gidan gyaran hali,amma da yake a nigeria muke.....kuma kura ma tasan gidan me babban sanda sai ya zamana dakatar da kamfanin kawai akayi sai bincike ya kammala. Bayajin zai iya bari maqiyansa su kalli faduwarsa da wurwuri haka,wannan ya qara masa qaimin shiga binciken da kansa gadan gadan. Ya fuskanci tarin abubuwa masu yawa cikin case din,wannna ya qara masa qaimi,bai kuma yarda yayi handling case din ma kowa ba. Duka da bacci da cin abincinsa qalilan ne. Amintattun experts investigators din daya aminta dasu kawai suke aiki ka'in da na'in,ba dare ba rana. Bai gayawa kowa abinda ake ciki ba banda anni da yace ta tayashi da addu'a,akwai matsala amma qarama ce ba wata babba ba,haka ya gayawa abba da farouq. Saidai sam hankalin farouq ya gaza kwanciya,don yana dawowa daga seminar dinsa ya biyo bayasa a washegari. Yadda ya ganshi ya tabbatar abun ba qarami bane,don ya nuna har a jikinsa don kuwa ya dan rame kadan saboda rashin bawa abinci muhimmanci. Ya sake sallamawa da miqa wuya kan muhamnadun yaci sunan muhammad din,namijin gaske ne da gaske......daga yadda ya tunkari komai yake gabatar dashi da dukka qarfin gwiwarsa da jarumtarsa kadai ya qara tabbatarwa NAMIJIN DUNIYA NE. Yanata qoqarin dodging komai farouq ya dubeshi. "4weeks without me dude.......have you noticed your appearance?.....check your reflection" Ya fada yana kama hannunsa zuwa gaban concealed mirror din dake wajen. Ya kalli fuskar tasa kaman yadda farouq ya buqata,sai ya saki murmushi ya miqa hannu yana shafa fuskarsa. "Chill out mana dude,nayi settling komai,It's come to an end......My evidence supports my claim....and it speaks for itself,all the fact are on my side,na gama komai gobe zasu saki kamfanin.....abu daya ya rage na gano shine,who's pulling the string" Hannunsa farouq ya riqo yana girmama qarfin jarumtarsa,yana jin inama ya samu irin wannan jarumtar tasa "We'll leave no stone unturned,we'll find him together" Rungume kafadar farouq yayi,yana sake jin qaunarsa cikin ransa. A gaba ya sakashi ranar,yasa ya ajiye komai tunda bincike ya kammala. Da kansa ya zauna ya masa gyaran fuska da sauran wasu abubuwa,yana masa suna hira yana bashi labarin nasa progress din da aka samu bayan seminar din. Duk duniya da farouq kadai yake irin wannan sakewar. Ranar duka tare suka qarar da ita,sai dare sannan kowa ya wuce makwancinsa,da zummar gobe da kamfani yaci gaba da aiki jibi tabbas dole su wuce gida,wanda sam bai fahimci meye ma'anar matsawar da farouq din yayi bama. Ya dauki wayar da zummar kashewa ya tarar da tarin miscalls da kuma saqonni,guda daya ya duba ya fahimci wacece. Fareeda ce....saqo bayan saqo kamar bata da wani sauran aikinyi sai tura masa da saqon. "How did she get ahold of my number?" Ya tambayi kansa da kansa. Tunawa da yayi da mahaifinta ya sauqaqe masa wahala,yasan samun numbersa zai zame mata wani abu kenan me sauqi. Tsaki yaja ba tare da yabi takai ba,ya kashe wayar ya kwanta. *_DUNIYATA LITTAFIN KUDI NE(PAID BOOK),KAI TSAYE KI TUNTUBI WANNAN NUMBER_* 08187255862 𝐃 𝐔 𝐍 𝐈 𝐘 𝐀 𝐓 𝐀 _ZAFAFABIYAR_ ̶B̶O̶O̶K ̶2 ⱧɄ₲Ʉ₥₳ 𝙋𝘼𝙂𝙀 29 29 ★Cikin kwanakin har ruwan jikinta takeji kaman ya qare saboda tsabar wani irin kadaici da dumbin tunani da yake cike a kanta. Sati hudu cur tana a cikin gidan......ba motsin kowa ba gilmawar kowa,ba hira da kowa,ba waya,daga ita sai tv sai karen gidan dake haushi nesa da muhallinta. Ada ko parlor din bata fitowa tana qunshe a daki,daga bisani ta fahimci depression na loneliness zai iya kamata,don haka da kadan da kadan ta fara fitowa tana zama. Saidai daga zaman sai bacci,sai wanka sai wata kwanciyar. Gyaran gidan kansa bai wani dameta ba,don tana ganin ba wani muhalli bane da zata damu kanta a kansa,hasalima a nata ganin waje ne da lokaci kawai take jira ta barshi. Abu biyu take gyarawa,bedroom dinta sai kitchen din da ba wani abun arziqi take dafawa ba. Tun ranar da tayi abincin safen nan rabonta da tayi wani cikakken abinci ta sawa cikinta,iyakar yunwa idan ta ciyota ta soya qwai guda biyu... Kota dafa indomie guda daya kota soya potatoes taci shikenan. A kwanakin tana jin yadda qirjinta yake riqewa amma taqi damuwa da wannan bare takai hankalinta kai,abu daya kawai take jira ya dawo,tayi duk yadda zatayi ta cika aikin maamah ta samu freedom. Ta sani tana da wata fitinanniyar ulcer data kusa sanyata tabi bayan mahaifi da mahaifiyarta bayan rasuwar ummensu. Ulcer data samo asali daga matsiyaciyar yunwar da tayi mugun horasu,takaita matakin da take xubda aman jini. Ta jima rabon data tashi,tunda ta samu sassaucin rayuwa suke iya ci su qoshi,amma a kwanakin nan da take bata alamu taqi maida hankalinta sam sam. ★"Alhamdulillah" Shine abinda ya furta lokacin da ya fito daga toilet wanda ya barshi wata guda cur kenan. Shirya kansa ya fara yi cikin butter milk color pyjamas yana tunanin kiran me sunan malam da ameh gobe kowa ya dora aikinsa a inda ya tsaya. Sam har ga Allah ya sha'afa da ita,abinda ya sameshi ya shafe abubuwa da yawa a kansa. Gidan duka ya masa datti a yadda yake tsantseni da tsananin tsafta,ya kammala shirin nasa sai ya kasa saukowa saboda gajiya,ya bude freezer dinsa dake dining area dinsa na sama yana fatan samun wani abun. Wuta ce 24/7 da kome zaka ajjiye a fridge din zaka sameshi fresh. Damammiyar fura ya ciro wadda ba komai cikinta daga nono din sai furar da aka markadasu suka hade jikinsu sosai. Furar daya samu ta masa daidai,don abace dame relaxing jiki da bada bacci me kyau da daddare saboda sinadaran da gero ke dauke dashi. Ta masa sanyi,baya kuma shan abu me sanyi sosai har haka,wannan ya sanya ya ajiyeta ya koma ya kunna tv don ya rage mintunan da zaiyi jiran furar. Kadan kadan takejin kamar wani baqon sauti cikin gidan sanda take baro kitchen inda ta soya qwai guda biyu,tana taraddadin ci ma saboda maiqon dake jiki amma kuma batajin tana da wani abinciii bayan shi. Fargaba taji tana cikata,wani irin matsanancin tsoro ya saukar mata. Sound ne tabbas wanda bata tantance na meye ba. To ko haurowa gidan akayi?,ko wani ne ya shigo ciki ya boye ba tare da sanin securities din ba?. Duka ba kalar tunanin da batayi ba,jikinta na rawa ta qarasa dakinta ta maida qofar ta rufe tana maida numfashi. Jin still da sound din sai tsoron yaqi barinta,ta taka da hanzari tabi duka windows din ta kulle sannan ta dawo tsakiyar dakin ta zauna tana raba ido tare da sauraron koma meye daga inda zai bullo. Sai data masa daidai sannan ya kashe tv din,ya dauketa ya hada da cup da spoon ya wuce daki. Sake kasa kunnenta tayi da kyau,a yanzu ba sound din,saita lumshe ido tana qoqarin saita nutsuwar kanta. Bata taba sanin kadaici masifa bane sai yanzu,bata taba sanin haka yake taba ruhi da rayuwar mutum ba sai yanzu. Wasu hawaye suka biyo ta lumsassun idanunta suka gangaro kan fuskarta. Gaba daya ta koma wata raguwa a kwanakin,zuciyarta kwata kwata ba wannan qwarin da tsaurin sai wani irin rauni da ya sake cikata,sai kawai ta kifa kanta saman pillow din ta saki siririn kuka,fried egg din da bata iya ci ba kenan. ★Bacci yayi sosai wanda da qyar ya tashi sallar asuba wadda duk tsanani zai wahala ta kubce masa. Koda ya koma yunwa ce ta tadashi,cikinsa gaba daya kamar an masa yasa. Yadan yamutsa fuska kadan yana tunanin me zaici?. Inda ameh yana nan ya tabbatar yanzun da yake qarfe sha biyu na rana ya gama breakfast yana jiran umarnin hada lunch da za'a kai company ko kuma ya jirayi zuwan dafa dinner. Brush ya fara shiga yayi sannan ya fito,ya dauki wayarsa guda daya a ciki ya kunnata. Kamar jira akeyi sabbin saqonni suka shiga turereniyar shigowa,baibi takai ba ya lalubi number ameh,bai sameshi ba,yaja dan qaramin tsaki,wala'alla ya lalata wayarsa kaman yadda ya saba,waya bata fiya dadewa a hannunsa ba zakaji ta fadi ko kuma ta lalace,wannan dalilin ya sanya ameh din kansa baida cikakken number boss din nasa,wanda dama kusan duk wanda ya mallaki number wayarsa ya cancanta kuma yana da connection dashi nakai tsaye irinsu ameh din dame sunan malam. Amna ya kira,bugu biyu ta daga. "Hamma......barka da dawowa" "Barka kade amna" "Good morning hamma......ya hanya ya gajiya?" "Alhamdulillah......ya makaranta?,kun fara shiga lectures?". Kai ta gyada "Mun fara hamma......ba dadi hamma ba supporter.......BB farouq yace na cika shirme......ya saddiq tsokanana yake koda kuna nan......nayi missing ya musaddiq har yanzu bai dawo ba......please hamma kace ya dawo haka?" Ta qarasa maganar a shagwabe. "Zai dawo soon" Ya furta badon yana nufin ya barshi ya dawo nan kusa ba. Tun tuni ya aike da musaddiq din wani aiki don ya nisantashi da maamah,bayason zamansa a nan ya tabbatar idan yana nan watarana maamah zataci galaba a kansa. Hakanan baison fitowa kai tsaye ya nunawa musaddiq komai akan maamah "Allah ya dawo dashi lafiya....." "Ameeen amneee......ki hadani da anni idan kin fito.....ki gayawa ameh lallai lallai yazo yau" "In sha Allah hamma" Tana shirin tambayarsa sabreen ya ajiye wayar.....saita bari kawai ta shigo gidan da kanta tayi mata barka da dawowa. Yadda taji yunwa na kama mata cikinta da gaske ya sanyata miqewa bisa dole. Yau kam sanye take da silk sleeping dress maroon color,riga ce iya cinya da wandonta dogo har qasa,saidai kuma tana da dan budadden wuya kadan. Duk da ramewa data danyi hakan bai hana rigar mata kyau ba,ta kuma zauna cif a jikinta. Jikinta ta jawo ta sauka daga saman gadon,tasa hannu ta tattare gashin kanta waje daya a qeyarta,ta taka a haka zuwa gaban madubi,ta jawo dan madaidaicin jewelry organizer din dake saman madubi ta budeshi,hair clip guda daya babba ta maqaleshi sannan ta samu vintage scarf ta daure kanta,wanda jelarsa dankwalin ta zauka kafadar hagu da damanta. Akwai socks a qafarta,wadda sanyin ac din gidan ya sanya dole take sakata saboda yadda marbles din yake daukan sanyi sosai,kwata kwata batasan ya ake controlling duka Airconditoners din ba bare ta daidaita shi,hakanan kawai take haquri. Sauqinta daya ana cikin yanayi na zafin farkon kasancewar damuna,banda haka ta tabbatar ba qaramar illa zatayi mata ba. A nutse ta murda qofar,ta fara leqo da kanta tukunna tana tuna motsin da taji jiya,sai data tabbatar shuru wajen yake ba alamun komai sannan ta fara fitowa a darare tana sanda hannunta dauke da plate din soyayyen qwan. Yau haka nan ya sauko da qafafunsa bai sanya takalmi ba. Fara tas din qafarsa dake da dogayen yatsu yake takawa a nutse yana sauka daga stairs din hankalinsa yana kan wayar da yake amsawa ta William,yanason sake tabbatar da komai na company din yana tafiya lafiya lau. Sanda ta buda qofar da zata sadata da parlor din farko ta sanya qafarta lokacin ya kusa da stairs din qarshe,wannan ya bashi damar ganin wulgawar mutum ba tare daya tantance waye ba. Dan tsam yayi da ransa sai kuma yadan qara hanzarin saukowar don yaga waye ya gilma din,sam zuciyarsa na masa nisa da tuna tana cikin gidan. Da wani irin sassarfa take qoqarin fita a falon ta sada kanta da falo na biyu na gidan ta boye kanta a kitchen. Murya takeji sosai tana sake kusanto inda take,tsoro ya sake cikata,kenan wani ne ya kwana a gidan akayi mata kwanton bauna?,har sai da akaji fitowarta sannan ya bayyana?. Ta shiga uku,su waye suka shigo?,abu daya ta sani ko zasu yankata su cinye ba wanda yasan sun shigo saboda tazarar dake tsakaninta da security din gidan. Tana saurin isa ga kitchen don ta buya yana sassarfar shan gaban macen daya gani. Kusan dukansu sai abun yazo musu lokaci guda,yana dab da cimmata tunaninsa ya dawo kansa. Ashe yabar wata cikin gida......akwai yarinyar dake rayuwa cikin gidan,wannan tunanin ya sanyashi tsaiwa cak,tsaiwar tasa ta bata damar wucewa kitchen din cikin matuqar sauri ta maida qofar ta kulle harda murza key. Qofar yabi da kallo yana zare wayar daga kunnensa. Mamaki kadan yana kamashi,anya qwaqwalwarta lafiya qalau take kuwa?. A nutse ya xura wayar a aljuhunsa yana dage kafadunsa cikin I don't care manner,sai kuma ya koma saman daya daga cikin kujerun ya zauna yana canza channel,kadan kadan kuma yana kallon falon. Ba wani tarkace bane ko wani abu a ciki,amma tsaftarsa bata masa ba. Ya saba duk inda ya wurga idanunsa ya ganshi fes yana qyalli da daukan idanu,amma a nan din idanunsa suna iya ganin qura a wasu guraren. Qaramin tsaki yaja can qasan ranshi yana fadin bazai dauki qazanta ba. Minti biyar yana jira yaga ta bude qofan amma ba alama,yunwa yakeji sosai,yana buqatar wani abu me nauyi da zai sanyawa cikinsa. Baya wasa sam da cikinsa,mutum ne me son lafiyayyen abinci musamman wanda ya dace da tsarinsa. Miqewa yayi ya taka a hankali ya isa bakin kitchen din,har a sannan tana maqale bayan qofar tana tunanin yadda za'a yi ta kubuta daga hannun mutumin da batasan yadda akayi ya shigo gidan ba. Knocking din daya fara yi a hankali ya sake gigitata,ta qanqame jikinta guri daya tana runtse idanunta hankali a tashe. Sau biyar yana bugawar ba wani motsinta,ranshi ya sake baci,sai kawai yabar wajen yana takawa a hankali ya nufi wata qofa daban da zata sadashi da kitchen din ta baya. *_DUNIYATA LITTAFIN KUDI NE(PAID BOOK),KAI TSAYE KI TUNTUBI WANNAN NUMBER_* 08187255862 𝐃 𝐔 𝐍 𝐈 𝐘 𝐀 𝐓 𝐀 _ZAFAFABIYAR_ ̶B̶O̶O̶K ̶2 ⱧɄ₲Ʉ₥₳ 𝙋𝘼𝙂𝙀 30 30 Jin an dakata da bugun ya sanyata sulalewa a wajen tana dafe qirjinta. Bata ankara ba hawaye ya balle mata,dama ta yaya za'a barta a gida irin wannan ita daya idan ba dama anyi shirin salwantar da rayuwarta bane da gangan. Tunda take a rayuwarta bata taba sanin tsoro na ainihi irin wannan ba. Qofar data hanga ya sanya taji relief,ta goge fuskarta ta mmiqe a hankali cikin sanda tana nufar qofar ko zata samu wata hanya da zata fice daga cikin gidan zuwa bakin gate. Tana miqa hannunta tana riqe handle din da zummar bude qofar daidai lokacin shima ya bude qofar da dan zafin nama,abinda ya sanyata ta biyo qofar takuma yi kyakkyawan masauki a jikinsa. Dif shi da ita wuta ta dauke musu,ita gaba daya tayi mutuwar tsaye je zuciyarta na wani mahaukacin bugu cikin saddaqarwa kan ta shiga hannun koma waye......yayin da shi kuma ba zatar fadowarta jikinsa ya sanya komai ya tsaye masa can na wucin gadi. Hannunsa ya sanya ya janyeta gefe yana hade rai da wani mugun miskilanci,ya hade girar sama data qasa yana dubanta sanda ta samu ta dafe kitchen cabinet din don ya taimaka wajen tsaiwa "What's this?" Ya furta a dake yana hade rai. Can qasan ransa yana jin haushi haushi yana saukar masa. Da biyu ta fada jikinsa ko meye?,ko tsabar sabawa da hada jiki da wasu ne?,a yanzun an turketa kusan wata guda ba tare da d'a namiji ba ta kasa daurewa?. "Ya kamata ki saita kanki,nan din ba irin sauran guraren da kika saba rayuwa bane....ki koyi controlling feelings dinki" Abinda yace da ita kenan yana takawa zuwa gaba hadi da miqa hannunshi yana bude drawers din sama. Sosai ta tattara dukka dauriyarta da nutsuwarta ta dawo da ita gangar jikinta tana ta kokawar hadiye tsoronta. Wani irin takaici ya kamata bayan data fuskanci shine. Ya akayi tayi gangancin gaza gane shine ya dawo?,bacin rai ya hanata komai,sai kawai ta juya tana takawa zuwa qofar data kulleta da hannunta ta fara bude key din da wani irin zafin nama. Duk da a rude take amma tasan sau biyu ta murza key din,yanzun ma sau biyun ta bude amma kuma data tura sai qofar taqi budewa. Sake murzawa tayi daya biyu har sau uku amma ba alamar qofar zata budu. Wasa wasa haka ta sake gwadawa amma jiya i yau,sai taji gudun zuciyarta na qara daduwa,don burinta kawai shine ta fita a kitchen din. Tayi iya duka qoqarinta amma ko gezau qofan baiyi ba,wannan ya sanya duk wani karsashi nata ya sulale,ta zame hannunta daga jikin qofar zuciyarta fal da tunanin ta yaya zata juya tabi ta daya qofar bayan yana kai kawo a kitchen din yana harkokinsa?. Duk wani motsi nata yana ankare dashi,har yadda ta dinga qoqarin bude qofar amma taqi koda motsi. Idanunshi jifa jifa a kanta sanda yake kai kawo tsakanin store din yana duba abinda zai iya sarrafawa da kuma dawowarsa kitchen din ya fara marinating kifi da zummar ya gasa shi,abinda ya manta rabonsa da yayi. Ya kammala cikin sauqi,saboda akwai komai kawai zubawa zaiyi ya saka a oven ya saita masa lokaci,sai ya saka din ya saita time ya koma ya jingina da kitchen cabinet din yana harde hannunsa a qirji yana jiran time ya cika yayin da yake sauraren voice note din da ya tarar daga William. Da fari baiko kalli sashenta ba koda sau daya kuwa,amma a hankali sanda hankalinsa yayi nisa da sauraren voice din sai kunnuwansa suka sauko masa raguwar sautin yunqurin bude qofar da taketa yi. A nutse ya daga idanun nan nashi dake da wani irin shape da yanayi me daukan hankali ya saukesu a bayanta daya fidda cikakken shape dinta saboda yadda kayan suka zauna mata cif da cif,daga kafafunta zuwa qugunta yayin da qugun zuwa cinyoyinta suka bude sosai suka bada wani faffadan qugu da yalwatattun cinyoyi. Vintage scarf din dake kanta ya zame ba tare data sani ba,saidai yana maqale a wuyanta,wannan ya sanya har clip din kanta pink color daya matse gashinta ya rage tsahonsa da yawansa ya bayyana. Baisan me ya maida idanunsa saman mazaunanta ba da suka bayyana sosai saboda silk material din dake jikinta,uwa uba kuma rigar bata qarasa rufe mata su ba. Abinda ya fara fado masa shine hirar amna da wasu qawayenta daya taba tsinta dake maganar maganin hips da sauran wasu hanyoyin qarawa mace hips. "Ita dinma ba zata kubuta daga amfani dasu ba......" Ya furta a ransa bayan da zuciyarsa ta tuna masa wacece ita?. "Allah ne yasan maza nawa ne suka taba kai hannunsu wajen,maza nawa ne suka taba taba wajen sukasan ya fadi da tudunsa yake" Wani mahaukacin tsaki daya cika kitchen din yaja,wani mummunan bacin rai yana saukar masa. Hannayensa ya saki kawai yana komawa zuwa bakin oven din yana jin zaman kitchen din yana gundurarsa. A duk sanda ya tuna iya shekarun haihuwarta a duniya da tayi kwata kwata na shekara ashirin da hudu cikin ta ashirin da biyar......da kuma adadin yawan mazan da akace masa takai qasa ko kuma ta taba mu'amala dasu,duk sai yaga ta masa baqiqirin,sai yaji wani abu ya tsaye masa a rai idan ya kalli koda gilmawarta ne "Idan tasan me yawan sha'awace me ya hanata ta fadi gaskiyarta a gida ayi mata aure?" Ya sake rayawa a ransa. Kwata kwata baya cikin jerin mutanen dake da ra'ayin riqau akan yaransu mata na sai sun gama karatu kafin a aurar dasu. Ya dauki izinina daga yadda yanayin halittarshi yake......wanda hakan yana daya daga cikin abinda ya sanya ya maida kwanyar da zata tsarta masa tunani na sha'awa a ransa cikin muguwar hidima da sabgar da idan ba mugun qaddara ba baida time da zata dauki wannan feeling din ta harba zuciyarsa har zuwa sassan jikinsa. Saboda kwata kwata bai shirya aure ba,totally mata basu taba burgeshi ba.....uwa uba bai tsara tsomasu a rayuwarsa nan kusa ba,saboda abinda yake kalla kusan dukkaninsu dukiyarka ko nasararka suke aure. (Kira gareku iyaye mata,a matsayinki na uwa ya kamata ki lura da yanayin kowanne yaro da kika haifa,don dukkaninsu ke kika haifesu,don kamanninsu daya hakan bawai yana nufin asalin halittarsu daya ba. Wani lokaci yaro namiji zaiyita nuna sha'awar aure,amma sai a masa caaa ace ya fiya tsaurin ido......wani lokaci yarinya na nuna wannan sai ace ta fiya rashin kunya da tsaurin idanu,ba tare sam da duba da cewa halitta bace daga ubangiji,sai kuyi mata mummunar fahimta,aci alwashin sai an turata jami'a,koshi yaran aci burin zuzzurfan karatu a kansa ko kuma sai yayi kudi. Kuskure ne wannan babban,daga namiji har mace idan aka fuskanci haka tattare dasu,idan tana da manemi nagartacce a aurar da ita yafi alkhairi,idan namiji ne yana da halin riqe kansa,ko kuna da wadatar riqe masa matar kafin ya qarasa zama mutum to a rufa masa asiri ayi auren a huta. Idan ba hali ko koya musu azumin litinin da alhamis,su lazimci karatun qur'ani,yawan tunasarwa da wa'azi,duk juyi kuma kada a dinga barinsu suna yawan kadaicewa a daki,a kusantasu da abokai na gari,da zarar dama ta samu kuma ayi a aurar dasu,Allah ya iya mana ya tarbiyyantar mana ameen summa ameen). Cikin sa'a ya samu ya gasu,sai kawai ya sakashi duka har aluminum foil din cikin plate,ya soma takawa yana hanyar ficewa ta daya qofar. Har ya kusa qofa sai ya fasa fitan,ja yayi ya tsaya sannan a hankali ya waiwayo,sai ya ware idanunshi a kanta yanata qoqarin kaucewa kallon guraren da yake ganin bai kamata ya kalla din ba. Cikin jikinta taji kamar da idanunshi a kanta,tuntuni taji ya tsaya da tafiyar da yakeyi abinda yake bata tabbacin bai fita din ba. Bata qaunar koda wanzuwarsu a waje daya sam shi da ita. Haushinsa takeji sosai,irin haushin da ko gilmawarsa batason gani ballantana qamshin turarensa. Cikin dakiya da jarumta ta soma takowa da zummar gewayeshi ta fice ba tare data yarda ta kalli ko gefen da yake tsaye ba ballantana tasan me ya tsaidashi din,tunda dai taga ya shigo ta nan din ta tabbatar hanya ce duk da bata taba bi ta nan din ba. Sai da tazo daf dashi zata gotashi din,cikin ba zata ya sanya qafarshi yana blocking duk wata hanya da zata wuce. Ta qasa ta kalli yadda yayi blocking din nata,wani abu ya sake zuwa yayi mata tsaye a wuya,sai take jin ta dauki iya abinda zata iya dauka daga gareshi,abun nashi kaman yanason ya qure iyakar haqurinta. Bashi da masaniyar kakkaifar katangar qarfe da garkuwar maamah a gareta shi yasa yake samunta a yadda ya so?,shi yasa yake samun daman juyata yadda yaga dama?,ko yana tsammanin izzarsa da dukiyarsa da sunansa duka su suka siya masa wannan. "Ka ban hanya zan wuce!" Ta fada adan zafafe tana jin zuciyarta kamar zata fashe. Duka abubuwan da yayi mata basu isheshi ba?,yanzun kuma sai ya qara da tarwatsa mata zuciya ta hanyar tsoratata?. Me yasa dole sai ya shiga harkan rayuwarta ne?. Hannunsa ya goye a qirjinsa bayan ya ajiye glass dish din da hake hannunsa yana dubanta. Kana kallon yadda Adams Apple dinsa ke sama da qasa kasan Shima nashi ran ya fara baci. Ya sake gasgata komai a kanta,yadda kunya ke nuna qaranci a tattare da ita. Yayi zaton zaizo ya sameta tayi laushi amma baiga alamun hakan ba. "Excuse me?" Ta kuma fada tana kafeshi da oily eyes dinta wanda ba kasafai ka fiya gane da qwalla a ciki ko babu ba,saboda koda yaushe yanayinsu tamkar an diga mai ko ruwa a cikin su haka suke. Kanta ta maida gaba ta hade jikinta sosai da zummar rabe masa,saidai ya hanata wannan damar,abinda ya sanyata sake tsaiwa kenan tana furzar da zazzafar iska daga bakinta. "Me kakeso ne?!......me kake buqata?,kome da kayi bai isheka ba?,ka kulleni for good one month.....kayi disconnecting komai da kowa daga gareni......yanzun kuma ka dawo kanason kasheni da tsoro?,me kake so?" Tayi maganar zallar bacin rai yana nuna kansa a fuskarta,tana kuma jin radadin abinda yayi matan da gaske. "Enough.....ya isheni!" Ta sake fada tana ware hannuwanta tare da fidda girman oily eyes dinta a kansa. "Am not your......." "Just stop!" Yayi maganar da muryar data ratsa har cikin kwanyarta,ta kuma sanyata runtse idanun dole "Am not your mate......dole kisan da wanne harshe zaki dinga min magana!" Ya sake maimaita mata a tsawace. Ji tayi kaman kanta bazai iya dauka ba,muryarsa tayi amsa kuwwa akunnuwanta sosai da kalar tsawar data manta rabonta da irinta,sai kawai ta juya da zummar koma yayane ya rabeshi ta wuce. Saidai kuma ina,yana ganin shirinta ya sanya hannu ya riqe hannunta da zummar dawo da ita da baya.....don dole ya fara saita mata harshenta kafin komai. Cikin rashin sa'a dukka maballan gaban rigar suka fara balle kansu da kansu saboda riqon da yayi mata. Abinda ya qara yawan adadin tashin hankalinta kenan jin iska ta fara ratsa ainihin fatarta,abinda yake tabbatar mata da cewa tabbas qirjinta tun daga sama zuwa qasa yana bayyana a waje. "Leave me.....ka sakeni!" Ta tattara qarfinta tana fada cikin tsawar da batasan ta yita bama saboda gigita da tsoron fitar tsiraicinta a gabansa,babban abun tashin hankalin da hannu daya taketa qoqarin kamo rigar saboda daya hannun yana riqe cikin nasa. Tsawar tata ya sake rura wutar fushin dake zuciyarsa wadda keta qissima masa abubuwa kala kala a kanta na irin hukuncin da zai mata. Ba'a saba masa rashin kunya haka ba,don haka baima san me ya dace yayi mata cikin zafin nan ba,sai kawai ya sake fincikota da qarfin da sai da taji hannunta ya amsa,batayi wata wata ba ta fada qirjinsa gaba daya. Bakinta yaqi mutuwa,ta tattara dukka qarfinta tana son tureshi tana bayyana tsantsar fushinta cikin maganganunta,ransa ke qara baci,zuciya kuma tana sake tunzurashi......yana da fushi yana da zuciya,amma ba kasafai ya fiya son tashin hankali ba "Shut your mouth" Ya fadi yana dubanta da kyau,saidai kaman bata ji ba,tana magana ne ransa yana baci,ya sakeyi mata riqon tsauri ba tare daya damu da son qwacewa takeson yi ba "Zip it....Hold your tongue" Still fushin da take ciki ya hanata gane me yake fada....zuwa lokacin hawayen da taketa tattalinsu sun fara yiwa kansu gurbi saman fuskarta. "Silence yourself......Don't annoy me!" Ya fada da husky voice dinsa......fushin da yakeji bayason ya bari yayi hukunci a irin wannan lokacin,don haka kawai sainya zabi riqe fuskarta cikin tafukan hannayensa da kyau yana furzar da iska me zafi daga bakinsa a saman fuskarta,idanunshi kan lips dinta dake magana suna rawa,sai kawai ya hade bakunansu guri daya. Wata irin tsotsa yakewa lips din nata cikin salon fushi da bacin rai. Tun a karon farko hankalinta ya fara dawowa kan abinda yakeyi saboda tsananin zafin daya ratsa lips din nata. A lokacin ne kuma ta fara yunqurin tureshi ta raba kanta da mummunan zugin da takeji saman lips din nata amma a banza,don ko motsawa baiyi ba,bai kuma rabu da ita ba sai daya tabbatar taji a jikinta,lips din ya ninka girmansa na asali......sannan yaja da baya yana dan tureta har sai data dafe kitchen cabinet. Qirjinsa sama da qasa yakeyi cikin mode na fushi da kuma mix na wani feeling da yaji yana ratsa tsakiyar fushin nasa. Gefe tayi da fuskarta saboda kuka daya taho mata sosai tana dauke dubanta daga cikin idanunsa da suka sauya launi. "Im not getting into it na zauna ina miki explaining ko doraki a hanya......i have many ways to punish you" Ya fada sautinsa yana rarrabewa kamar wanda yayi tseren gudu ya gaji,sai ya fusgi dish dinsa yana ficewa daga kitchen din. Duk da tasan ya fice din amma ta gaza dago kanta,don jikinta ta tabbatar rawa yakeyi ko ta ina. Sai data kusa minti daya sannan ta motsa da nufin fita itama tacan,amma sai taji QIT kamar an cire maqullin jikin wannan qofar aka murda handle din aka bude sannna aka juya ana barin wajen. Ko daga qamshin turarensa kawai ta gane shine ya bude,batayi wata wata ba ta qarasa wangale qofar ta kuma taka tana fita ba tare da ta tsaya tantancewa da mutum a falon ba ko kuma babu. *_DUNIYATA LITTAFIN KUDI NE(PAID BOOK),KAI TSAYE KI TUNTUBI WANNAN NUMBER_* 08187255862 𝐃 𝐔 𝐍 𝐈 𝐘 𝐀 𝐓 𝐀 _ZAFAFABIYAR_ ̶B̶O̶O̶K ̶2 ⱧɄ₲Ʉ₥₳ 𝙋𝘼𝙂𝙀 31 _Daga abdullahi dan abbas R.A,wata kuyanga(baiwa)budurwa tazo wajen manzon Allah S A W,ta gaya mishi cewa,babanta yayi mata auren dole,sai manzon Allah S A W ya bata zabi(haquri da auren ko a raba)_ _____________________________ 31 Idanunta a rurrufe ta tura qofar dakin nata ta shiga,ta kuma maida key din ta rufe tana jin kamar zai sake biyota ne. Wani azababben kuka ta saki tana jin yadda labbanta ke wani irin zugi kamar zasu cire daga saman bakin nata. Tako ta ina tun daga saman labban nata har zuwa fuskarta dama qirjinta ba abinda suke fitarwa sai wannan mayataccen qamshin nasa. Ta jima tana kuka gami da murza lips din,tana fatan zugin da takeji ya ragu.....har batasan iya adadin lokutan data shafe a haka ba. Qarar agogon dakin ya sanyata maida idanunta da sukayi mata nauyi saman agogon,lokaci yaja.....saita miqe da dan hanzari ta zauna. Kaman yadda jikinta bai daina rawa ba haka zuciyarta da labbanta basu daina mata zafi ba. Duka hannuwanta ta saka ta rufe fuskarta dashi tana ci gaba da sauraren bugun zuciyarta. "Ba lokacin wannan bane sabreen.....ba lokacin bata lokaci bane wannan,kina sake bawa maamah damar kasancewa da 'yan uwanki ne kawai a kowacce daqiqa....lokacin aiki ne tuquru yanzu don qwatar kai.....ki daina bari normal halittan namiji kamar saura yana firgitaki......wanne iri ne baki gani ba?" Taji ana gaya mata daga can wani sashe na zuciyarta. Abinda ya zaburar da ita kenan ta fara zame kayan baccin jikinta ta daura towel ta wuce bandaki. Wanka tayi ta dawo ta shirya cikin atamfa doguwar riga,ta gyara ta matseshi cikin hair tie masu wani irin adon stones masu garai garai a jikinsu dan madaidaita. Bata saka komai a fuskarta ba,amma tayi wani irin kyau duk da ramar da tayi,saidai kuma fatarta tayi fresh saboda zama waje daya da rashin bawa rana damar qona fatarta,uwa uba har yanzu mayataccen gyaran jikin nan yana nan baibar jikinta ba,batasan wanne irin rantsatsen hadi bane annin ta biya kudi akayi mata. Duk da yunwar dake qwaqular cikinta amma sai taji sam ba zata iya zama ba,hasalima duka tasirin yunwar ya gushe,kitchen take da muradin shiga ta shirya abincin dare,wanda take fatan koda batayi na rana ba aqalla a samu na dare. Da dan hanzarinta take fitowa daga hallway din,hankalinta yayi gaba zuwa kitchen sautin muryarta ya dakatar da ita "Adda sabreen" Amna da shigowarta kenan ta fadi fuskarta cike da murmushi. Suna hada idanu ta sakar mata fuska da salon nata murmushin. Haka kawai tana tuna mata da huda duk da hudan miskila ce ba kaman amna ba,amma sai take mata yanayi da hudan. "Yaushe kika shigo?,afwan ban sani ba ina ciki ina wanka" Ta fada tana neman gefan wata kujerar daban ta zauna. Da murmushinta tace "Adda sai an miki uzuri,matafiyi ba'a rasashi da gajiya a jikinsa,ni har zan kunna wayata ma na duba wani assignment kafin ku samu fitowa" Kyawawan fararen idanunta sabreen ta fiddo waje. "Haba dai,ya zaki zauna kiyita jira,da kin qarasa kinmin magana ai". Bakinta ta rufe da tafin hannunta "Kinaso hamma ya ballan qafa?,ba'a shiga shiyyar dakinsa direct ai,BB farouq ne kawai ya isa". Tabe baki tayi a fakaice,can qasan ranta tana fahimtar tsananin izza gareshi da shegen mulki. Fara sako mata zancansa da tayi yasa sabreen miqewa cikin qarfin hali da son nuna komai lafiya "Bari na baki ruwa kisha" "Am full adda.....saidai na rakaki kitchen naga kaman kitchen zaki shiga" Kafada ta daga da murmushi "Alright.....muje" "Yau hamma za'ayi full da abincin addana.....yadda yakeson abinci me dadi na tabbatar adda na ba daga baya ba.....in fact ma tunda har kikayi nasarar samun hamma na na tabbatar komai kin hada" Tayi maganar da dariya dariyar tsokana. Bata ce mata komai ba,tadai qoqarta sauke mata murmushi kawai. Sanda suka shiga kitchen din duk sai taji ta takura,ta rasa ta inda zata fara,saboda idan maganar qwarewa ake ta fannin girki tasan bata cikin jerin wadannan matan,infact ma ita ba gwanar shiga kitchen bace sam.....to ina ma taga time?,tana ta abinda qannenta zasuci susha su lulluba sutura,suyi magani idan lalura ta taso?. Tasan huda ta tsere mata sosai ta fagen iya girki,don tun tana fita tana barinsu hudan tana musu tsumburin burin har tazo ta qware. "Kaman ya kamata kiyi surprising hamma na ko?" Amna ta fadi da murmushi tana duban sabreen. Kallonta kawai tayi kallon dake nuna alaman tambaya,sai amnan ta daga kafada "Gift dina na yau zan gaya miki best food nashi da daddare.....but nima zaki bani tukuici ki gayamin sirrin skin dinki adda don Allah?" Ta qarasa fada a shagwabe. Abun dariya yaso bawa sabreen saidai batayi ba illa murmushi data saki,ta kalli fatar tata ta kalli amna,ita bataga wani kyau da fatarta tafi ta amna ba "Seriously adda kina burgeni at the first time dana fara ganinki.....kawai naji jinina ya hadu da naki" Ta fadi da gasken ta yadda a furucinta zaka fahimci da gasken take. Kusan tana zaune amna ta hada duka ingredients din na kalar abincin. Ta miqe tana daura apron data gani tana bawa amna daya,sai qararrawar dake kitchen din ta dauki tsuwwa. Amna ce ta duba,saita waiwayo ta kalleta "Kira ne daga bakin gate" Tayi maganar tana miqa mata wayar "Ki daga" Tace da ita,ba musu ta saka a kunne,bayan wasu sakanni ta dawo da dubanta kan sabreen "Wai baqi ne dake.....zuwaira daga wajen hajiya mariya maamah". Maganar taji ta bugu qirjinta don tazo mata kamar a bazata,sam ta mance da issue dinsu,sai ta fara zare apron din tana cewa "Kice a barsu su shigo" Yadda ta fada mata haka ta gaya musu,ta zare apron din ta ajiyeta ta soma dosar kitchen din tana cewa "Ina zuwa amna" "Ba damuwa adda" Ta amsata tana matsawa kitchen din don ci gaba da aikin. Kasa tsaiwa tayi daga cikin parlor din,ta taka har qofar qarshe wadda daga ita sai balcony din da zaka sauka zuwa farfajiyar gidan. Tsaye tayi kawai riqe da qofar,ba abinda ya hanata hango wajen sai lafiyayyen curtain din daya raba tsakaninsu. "Assalamu alaikum" Muryar zuwaira ta fara rasa falon kafin ta bayyana Laila na biye da ita a baya da luggage dinta dake da girma,tana takawa d'ai d'ai,tana sake ganin alatun da aka xubawa gidan,sai take ganin wancan zuwa bataga komai bama. "Wa'alaikumussalam" Ta amsa mata idanunsu yana haduwa waje daya dana laila. Wata faduwar gaba ta saukarwa lailan lokacin da idanunta ya shiga cikin na sabreen dake tsaye tana jiran shigowarsu "Kambu.....who's she?" Ta samu kanta da furtawa a qasan zuciyarta saidai kuma labbanta a sarari ma rawa sukeyi. Yanayin kallon da lailan ke mata sam baiyi mata ba,a nutse da wani irin jan aji ta debe kallonta daga kan lailan tana maidawa kan zuwaira dake qoqarin gaidata "Basai kin tsuguna ba......ta nan ga qofa nan a nan din akwai dakuna a ciki,ku zabi duk wanda yayi muku" Ta amsata a taqaice don ko tsaiwarsu a wajen sai taji bata qauna. Tasan da qofar ne cikin ranakun zaman kadaicin data dinga yi cikin gidan *_DUNIYATA LITTAFIN KUDI NE(PAID BOOK),KAI TSAYE KI TUNTUBI WANNAN NUMBER_* 08187255862 𝐃 𝐔 𝐍 𝐈 𝐘 𝐀 𝐓 𝐀 _ZAFAFABIYAR_ ̶B̶O̶O̶K ̶2 ⱧɄ₲Ʉ₥₳ 𝙋𝘼𝙂𝙀 32 _Daga abdullahi dan umar R.A yace."manzan Allah S A W ya hana auren shigaari,shi kuwa auren shigaari shine,mutum ya aurar da d'iyarsa ga wani,bisa sharadin Shima wancan zai aura masa tasa 'yar,kuma babu biyan sadaki a tsakaninsu(musanye kenan)_ _bukhari da muslim ne suka rawaito_ ___________________________ 32 Tasan qofar ne cikin ranakun zaman kadaicin data dingayi cikin gidan da kuma Yanayin wajen kuma tasan guri ne baqi na kusa bayan boys quaters da gidan ya mallaka na musamman da yake daga can bayan gidan. Bata da matsala dasu,koda dakunan hallway suka zaba kuwa,don kowacce rana a lissafe kwanakinta cikin gidan suke. "To.....to madallah......bari mu qarasa" Xuwaira ta fada tana wucewa gaba laila tana biye da ita. Duk wani taku daya biyu na lailan saisun hada idanu da sabreen din wadda ke tsaye yana karantar yanayin kowanne a cikinsu. Dauke dubanta tayi,sai ta koma saman kujerar falon ta zauna kawai yanayin jikinta yana neman sauyawa. "Assalamu alaikum" Muryar zuwaira ta sake ratso falon. Idanunta ta daga a hankali tana duban zuwaira sanda take takowa falon riqe da waya a hannunta fuskarta a sake "Ranki ya dade.....hajiya nason ganawa dake" Tayi maganar tana miqa mata wani qaramin akwati da sabreen din ta kasa amsa sai binsa da kallo da tayi. Daya hannun waya daya akwati,kuma dukkaninsu idanun zuwaira suna gaya mata ana da buqatar karbar kowanne. Cikin kwanyarta taji ana umartarta data karba,ba wani laka a jikinta ta karba dukkaninsu "Sirri yana da matuqar muhimmanci......hajiya nason sirri matuqa" Ta tsinci muryar zuwaira tana gaya mata. Idanu ta waiwayowa ta zubawa zuwairan,sai kawai ta dauke kanta tana nufar hanyar hallway don komawa dakinta. Kaman ana jira ta shiga dakin wayar tahau kadawa,ta zubawa sunan da zuwaira tayi saving dashi wato hajjaju. Tattaro dukka wata dauriya tata tayi,ta hadiye wani yawu me kauri sannan ta daga kiran ta sakashi a hands free hana ajiye wayar saman cinyoyinta. "Ka kula da ita.....huda kuje ya baki magani kisha kafin ki kwanta.....sannu qawata". Abinda kunnuwanta suka fara jiye mata kenan wanda ya sanya tsigogin jikinta tashi. Ta runtse idanunta tanajin kamar an daukk guduma an kwada mata saman kanta. "Huda kuma?" Ta motsa labbanta tana furtawa a wahalce. Murmushin maama ne ya soma riskarta kafin tace "Eh,huda.....ko bazatayi lalura ba?......kowanne sakaci da zakiyi akwai sakamakonsa kan halittar da kika fi so fiye da komai da kuma kowa......" "Bani huda din" Ta fada kanta tsaye da wani irin yanayi me kaushi. Wata qaramar murmushi me kama da dariya ta saki "Da wuri haka?,zabin cetonsu ai yana hannunki tunda na gabatar miki da dukka kayan aiki.......bansan me yasa kika yanke sadarwar dake tsakaninmu ba.....saidai koma meye wannan ba damuwa ta bace......kowanne ganganci kuskure ko sakaci sakamakonsa rubutacce ne a nan......" "Idan kikayi kuskuren cutar da ko farcen daya daga cikinsu ne......to lallai ba shakka ba mallaka miki danki zanyi ba......zan sadar dashi da kabarinsa ne,zan mallakaws barzahu shi a madadin ki" Sabreen ta fada cikin tsawa da wani irin birkitaccen sauti daya ratsa maamah,taji kuma har cikin jikinta da gaske ta fadi maganar. Ta danyi jim kadan tana jin wata shakka tana ratsa ta,sai kuma ta saki wata dariya "Bismillah mana......indai har kina ganin hallaka mutum kamar muhammad jadda abune me sauqi....." "Akwai abinda yafimin wannan sauqi?.....aikinki ya ninka shi wahala sau dubunnan da bazasu qirgu ba.......idan naso a safiyar gobe za'a wayi gari da sanarwar jana'izarsa hajiya maamah.......saboda haka ki kula......akwai kadarata a hannunki......a nan kuma akwai ruhinki dama kadararki gaba daya a tare dani" Daga wannan ta yanke wayar. Zare wayar daga kunnenta maamah tayi tana kallo. Wani irin mamaki da tsoro yana kamata,wacce irin yarinya ce wanannan?,wadda bata tsoro ko shakkar duk wani abu girman tsoron dake tattare dashi?. Gabanta yayi mummunar faduwa sanda ta tuna zancan idan taso za'a sanar da jana'izar fu'ad din a gobe. Ta motsa da wani irin hanzari ta miqe sai kuma ta koma ta zauna. Waye zata gayawa?,shi fu'ad din?,tace yakula da za'a iya kasheshi?,to waye zai kasheshin?,ya kuma zatayi masa bayani akan yadda akayi ta sani?,ya daina cin abinci?,wannan kuma shine burinta babba a yanzu ya karbi abinci daga hannunta don samun cikar burinta,ta yaya zata sanya idanu akan wani abu daban da zata shirya wanda zai sauka daga kan tsari da kuma muradinta?. Zuwaira ce ta fado mata rai,sai taji tana samun sassaucin tsoron da kuma firgicin da take ciki. Hannunta dukka biyun ta sanya ta dafe kanta. "Huda,ya kula da ita ya bata magani tasha?,who's she?" Abinda ta dinga maimaitawa kenan. Hudan da har yanzu take ganin tana buqatar therapy tana buqatar counselling akan mikin da nasir yayi mata.......yanzun kuma tana shirin sake fadawa wani abun na daban?,kanta da zuciyarta kuwa zasu iya dauka?,ya kamata ta ciyar da d'anta ta kowacce siga muradinta.....idan yaso in taga dama bayan ta mallakeshi ta yayyankashi ta cinye. Abu daya ta kasa jurewa ya kuma gaza barin zuciyarta huda,ta yaya zata ji muryarta?. Bata taba jin dauke wayoyin ya dameta ba irin yau,ta dinga jin kamar tayi hauka idan ta tuna ba wata sauran hanya da zata iya samun damar magana da huda. Sosai tayi qoqarin ganin amna bata gane komai akan fuskarta ba. Ta kama mata aikin sukaci gaba dayi,tana ci gaba da mata hira tana bata labarin fu'ad. Kwata kwata bata jinta ma ballantana ta fahimci abinda amna din ke fada,a haka suka kammala amna ta fito tabar mata kitchen din. Sosai ta zazzaga dukkan abinda ya kamata ta sake juya abinci ya koma ainihin launinsa. Ta tsaya kaman ko yaushe ta zubawa abincin idanu zuciyarta na wani yamutsawa,mafi rinjaye na zuciyarta tana jin kamar wani yanayi mara dadi,wani yanayi da yafi kama da rashin jin dadi?,rashin kyautatawa?,ko aikata abinda ba daidai ba?. Itama bata sani ba,bata taba zaton da hannunta zata iya ciyar da kowanne dan adam abinda bai kamata yacishi ba......saidai abu daya ta sani shine....itadin guba ce ga duk wanda yace zai kawowa innocent rayukan nan guda uku farmaki. Takun da taji dake alamta mata an shigo kitchen din shine abinda yayi bala'in razanata. Da sauri a kuma birkice ta daga kanta tana duban me shigowar. Zuwaira ce fuskarta da murmushi ta qaraso cikin girmamawa. "Afuwa,dama cewa nayi bari nazo naji ko akwai aikin da za'a kama miki?" Tayi maganar tana duban warmers din da a gaban idanunta tana labe sabreen din ta cika aikinta tsaf. Idanunta ta lumshe tana jin yadda zuciyarta ke bugawa,sannan ta tattaro dukka qarfinta ta bude idonta akan zuwairan "Wannan shine kuskurenku na farko,bana buqatar ki sake shiga wani guri a cikin gidan nan ba tare da kin tsaya kin nemi izini ba an kuma baki" Kai ta rusunar "Ayi haquri bazai sake faruwa ba in sha Allahu" Bata iya amsa mata ba,sai kawai warmers din data mata nuni dasu "Ki kaisu kan dining" Tayi maganar tana dosar qofar fita a kitchen din,don sam bata da qwarin tsaiwa ci gaba da magana. Tana sanya qafafunta da zummar fita tana sako tata qafar abinda ya sanya suka kusa karo da juna,yatsun qafarta suna caki na sabreen haka gwiwarta saita tsaya cak bata ja baya ba bata kuma koma ba. Tsaiwa cak itama sabreen din tayi tana danjin qafarta na dan radadin kadan saboda qafafunta akwai alamun tana ajiye farce. Shirun da sabreen din taji ya sanyata daga kanta ta sauke dubanta akan laila. Tana tsaye cak ba alamun zata kauce mata ta bata hanya. Bisa dukkan alamunta tana jiran sabreen ne ta kauce mata,kota koma sai ita ta wuce. Cikin qasa da second biyu sabreen din taji wani abu ya saukar mata,wani abu me kama da izza da jin mallaka ya mamayeta. Ta lumshe idanunta sannan ta zubesu fes akan laila tana duban tsakiyar qwayar idanunta da wani irin kallo dake qure qarfin halin mutum. Da farko itama laila din ta zuba mata idanu,saidai a hankali wani kakkaifan abu ke ranqwafar da nata idanun. A hankali taji ta gaza jurewa,saita dauke dubanta daga kan sabreen din tana ja da baya,ba tare data sake dubanta ba ta rabata ta wuce a tsanake ba tare data sake duban sashen da take a tsaye ba. Da idanu tabi sabreen din har ta wuce,ta maido dubanta cikin kitchen din tana jin kamar yau karon farko ta tozarta......a karon farko taji wata 'ya mace tayi mata kwarjini,har kuma ta juyata ba tare data furta kowacce kalma daga bakinta ba. Hada ido sukayi da zuwaira,sai zuwairan ta tabe baki tana dauke kai. Cike take dama da lailan,cike kuma take da yadda maamah ta dinga jaddada mata ta girmama lailan,don gidan fu'ad a wajen lailan tamkar gidan mahaifinta yake,tammar kuma gidan yayanta da suke uwa daya uba daya yake. "Idan me guri yazo dai me tabarma nadeta yakeyi,nan din dai akwai macen data amsa sunan matar gidan,komai ayishi bisa takatsantsan". Sarai ta fahimci abinda zuwairan ke nufi,amma sai taga sam bata da lokacinta,don abinda sabreen tayi yafi tsaye mata a rai,yadda zaiyi handling nata. Da gaske komai na gidan yayi mata,da gaske zuwa yanzu tanaso ace itace mamallakiyar gidan. Ta cika gidan da izzarta da mulkinta da kuma ikonta kwatankwacin hajja,tako ina ta zama ME MULKIN gidan. Samun amna tayi tana shirin tafiya. "Har me?" Ta fada cikin nuna kulawa. Murmushi ta saki "Driverna na aje adda tun dazun fa,daga cewa anni zanzo na miki sannu da zuwa". Fararen idanunta da a yau take jinsu wani iri ta kada,bata da energy din dogon magana. Closet dinta ta bude kawai tayita fiddo abinda take ganin ya kamata ta bawa amna. Ta hada abubuwa cikin qaramar jaka me kyau da daukan hankali. Ido amna ta fiddo tana nuna tsananin murna da mamaki "Duka adda?" Ta fada da murmushi. Abun ya burge sabreen sosai,yadda amna din ta nuna,duk kuwa da cewa tasan tafi qarfin duka abinda zata bata din. Fitowar zuwaira da laila daga kitchen din ya danja hankalin amna dake qoqarin ficewa,ta bisu da kallo kawai kafin ta juya a hankali ta fara takawa tana fita daga falon. "Sai haquri ranki ya dade....laila kenan..... D'iyar hajja harira.....hajja harira 'yar majalissar zartarwa hajiya mariya maamah". A badini kyakkyawan masauki maganar zuwaira ta samu,hajja hariran da sukayi tattaki har cikin gidansu suka kai qudurin aurota don su cimma buqatarsu?,ta yaya zata manta wadannan fuskokin,ranar,dama abinda ya faru a ranar....har maamah din tana da qarfin halin ajiye budurwa irin wannan a gidan d'an data haifa?,wanne irin kwado ne wannan?,budurwar da babu wata alaqa tsakaninsu face ta zallar qawancen dake tsakaninsu?,a tsarin abota da mu'amala da zata fishshi dan adam tasu bata kan ko guda daya. Kai ta jinjina,information din ya mata kyau da ma'ana,amma kuma batajin zata sakewa zuwaira ko ta nuna jin dadin hakan. "Ya kamata ki dinga tsaiwa a iyakokinki kawai" Abinda tace da ita kenan tana takawa zuwa hallway dinta don komawa dakinta,duk da har yanzu ba wani cikakkiyar nutsuwa ko sukunin data samu daga uban tunanin dake addabarta,gefe guda kuma tana cike da fata da fargabar sanya abincin a bakinsa ya zarce zuwa cikinsa. *_DUNIYATA LITTAFIN KUDI NE(PAID BOOK),KAI TSAYE KI TUNTUBI WANNAN NUMBER_* 08187255862 𝐃 𝐔 𝐍 𝐈 𝐘 𝐀 𝐓 𝐀 _ZAFAFABIYAR_ ̶B̶O̶O̶K ̶2 ⱧɄ₲Ʉ₥₳ 𝙋𝘼𝙂𝙀 33 _Daga nana Aisha R.A tace:manzon Allah S A W yace:Duk matar da tayi aure ba tare da izinin waliyyinta ba,to aurenta batacce ne,idan mijin ya tare da ita taci sadakinta saboda halastar farjinta a gareshi_ 33 ★"ma sha Allah,sannunta da qoqari" Anni ta fada sanda ta gama ganin kayan da amna ta kawo wanda sabreen ta bata. "Tana da kirki anni......amma sai nake ganin hamma me irin halinsa ya dauko,she's so quite,batason hayaniya da yawa,bata fiya bada amsa ba ko magana,tafi yawan murmushi kawai". Murmushi anni ta sauke,har zuciyarta tana sake jin yarinyar tayi mata,a duk wani lokaci da maganarta zata tashi tana sake jin sabreen ta kwanta mata ne. "Ai dama sai hali yazo daya ake iya zama ko?,Allah ya qara hada hankulansu......yauwa farouq yayi nemanki kuwa sanda kika fita......naji kaman yana maganar zaku abuja passport dinki yayi expired,za'a sake miki wani". Idanu amna ta fiddo sannan ta qanqame anni "Anni hala Lokacin tafiya ya kusa?". Dan tureta kadan tayi daga jikinta "Gashi kuwa kin gani keda tafiye tafiye basa isarki" Dariyar jin dadi ta qyalqyale dashi. "Amna wannan tafiyan daban yake a rayuwata Allah,ba wani trip da yakaimin wannan dadi....whole family fa anni.....wannan karan kuma abun zaifimin dadi saboda nima na samu partner addana,adda sabreen,na daina maqalewa su ya saddiq suna wulaqantani,wannan karon tafiyar zai zama na musamman" Tayi.maganar with full excitement. Da kallo kawai amna ta bita kafin ta saki murmushi,ita kanta tasan tafiyar zata qara dadi musamman da idanunta zasu dinga gane mata fuad dinta da iyalinsa a gefe,cikon mafarkinta kenan "Anni bari naje na sameshi" Ta fada tana daga yatsunta gami da lissafa watan da tafiyar tasu zata kama "Yes" Ta furta tana jin farinciki yana lullubeta,saita cilla da sauri zata fita tana cewa "Dis time har abba fa sai na karbi kudin tsaraba a hannunshi,komai bibbiyu zan dinga siya nida addana" "Kunfi kusa ai" Anni ta bata amsa. Dakatawa daga fitar da anni taga amna tayi shi ya sanyata daga kai tana dubanta zuciyarta cike da tambaya. A sanyaye taga amna din ta dawo tana zama gefanta "Lafiyarki ke kuma?" Ta tambayeta tana nazartarta da kyau "Wani abu na gani anni a gidan hamma". Jin an ambaci fu'ad din ya sanyata tattara hankalinta akanta "Me kenan?" Ta amsawa amnan cikin zuciyarta tana fatan ba wata matsala bace a tsakaninsu. "Anni.....me aikin gidan maamah na gani,ita da wata budurwa......bansan budurwar ba amma tana kama da wannan qawar maamah din aminiyarta dinnan....." ".....hajja harira" Anni ta samu kanta da fada ba tare data shirya ba "Eh ita" Ajiyar zuciya anni ta fesar "To shine me amna?" Ta furta cikin hikima. Tun asalin tarbiyya anni irin matannan ne da basa bari yaro yana kawo musu hira ko maganar wani guri. Qasa amna tayi da idonta "Ba komai,kawai anni ji nayi jikina bai aminta dasu ba,daga yanayinsu fa anni kamar a gidan zasu kwana fa,qilan ma komawa gidan sukayi Allah anni". Ta fada tana bata rai. Da kallo tabi amnan,amna din ba yarinya ce qanqanuwa har can can ba,kome ake ciki ko yake faruwa tabbas dole tana gani tana kuma fahimta. "Hammanku majibancin lamura da jama'a ne,bazai zama abun mamaki ba idan anga sabbi ko baqin fuska a gidansa ba,kedai kici gaba da taya dukka 'yan uwanki da addu'a". Kai kawai amna ta gyada ba tare data samu cikakkiyar gamsuwa da bayanin anni ba,ta miqe tana fita daga dakin kamar yadda tayi niyya da farko. Fitar amna dukka sai hankalinta ya dawo jikinta,sam sam taji bata gamsu da wanzuwar zuwaira da waccar yarinyar a gidan ba. Tasan wacece maamah,tasan kuma dukkanin wanda ya rabu da ita yaya dabi'arsa zata iya kasancewa. Indai da wata manufa ko wani qullin daban aran maamah din,muddin tana raye ba zata taba bari haqarta ta cimma ruwa ba. Koda ta dauke idanu akan abubuwa da yawa,koda tayi kawaici akan abubuwa masu yawa....amma a nan ba zata bari ba,ba zata bari tabi fu'ad har rayuwa cikin gidansa ta ruguzata ba. Saita jawo wayarta tana qoqarin danna kiran. *SABREEN* Batasan adadin sau nawa ta leqa dining din ba da zummar ganin ko ta samu nasara ya taba kayan abincin?. Saidai a duk gewayen da zatayi bataga wani alamun taba komai ba cikin kayan dake danqare a table din ba. Ba iya yaci abincin bane kawai damuwarta ba aah......tanaso tayi amfani da wannan damar ta karbi wayarta a hannunsa,tanaso duk yadda za'a yi ta samu cikakken bayanin yadda su hudan suka koma qarqashin kulawa da mulkin maamah. Abun yana tsananin daure mata kai......ta yarda da momma bahijja....ta kumayi imanin haka siddan ba zata bari haka ta faru ba,duk dadai ma batasan ainihin wacece maamah din ba. Sam bata sako kawu rufai a ciki,shikam tasan ko ya fita sanin wacece mariya to zai aikata fiye da hakan ma. Zuwa sha daya na dare haqurinta ya gaza,ta miqe da wani irin kaiwa maqurar haquri tana yafa mayafinta saman doguwar rigar jikinta ba tare data buqaci dankwali ba ta sanya slippers dinta tana bude qofar dakin ta fice. Kamar magen dake kwanton farautar kamun bera haka ta dinga tafiya a hankali tana durfafar stair case din dake facing dinta. Duk taku daya sai bugun zuciyarta ya qaru,amma kuma tuna huda nadra da haneefa kadai ke qara mata qwarin gwiwa. Tana jin a kansu zata iya komai,zata kuma fuskanta da tunkarar komai da kowa. Cak ta tsaya a stairs din farko tana jin kaman wanda ke kusa sosai da ita idan ya qurawa qirjinta idanu zai iya ganin yadda zuciyarta ke bugawa ma. "Shi waye?,mutum ne kamar kowa,mutum ne kamar ni,bashi da wuta bashi da aljanna,bai isa kuma ya yankani ya cinye namana ba" Ta gayawa kanta da kanta murya can qasa qasa dukka tana zaton BUGUN ZUCIYARTA zai daidaita. Aqalla ta tsaya jiran mintuna kusan goma amma still ba abinda ya canza,sai kawai ta runtse idanunta ta kama makarin stairs din ta fara haurawa saman da wani irin confidence da batasan daga inda ta aro shi ba. Idan ba jikinta da hancinta ne ya mata qarya ba,to tabbas atmosphere da weather na wajen daban yake dana kowanne bangare na gidan. Wani irin lullumsan yanayi da wani irin kebantaccen qamshi da bata taba jin makamancinsa ba. Bata taba lura da cewa shimfidadden carpet bane kan stairs din sai a yanzun da qafafunta ke barazanar nutsewa a cikinsa. Bayan qafafunta sun nutse din kuma wani irin sassanyan yanayi tafukan qafarta ke riska a can cikin carpet din. Duk yadda taso jure qauyancinta amma abun yafi qarfinta,dole ta dinga bin carpet din da kallo har zuwa sanda ta riski wata pivot door wadda gefe da gefanta duka glass ne da bazaka iya hango ainihin parlor din ba,yayin da daga tsakiya ta kasance ta gogagen katako da aka yima design na zamani wanda ya maidata smart door. Tun daga zubin qofar tasan wajene na musamman kuma kebantacce,ta bangare guda kuma taji dadin samun qofar a bude,banda haka da sai tayi tsaiwar da qofar zata gama tantance wace kafin ta bata daman shiga parlor din. Mutum ne shi me wani irin jiki wanda baya qaunar zafi tun asali,saidai duk da hakan tsananin kare lafiyarsa ya sanya bai fiya kwararawa kansa A.c ba. Duk wanda ya sanshi ya sanshi da wannan dabi'ar na kaucewa abubuwa masu sanyi ciki kuwa harda ac din. Zaune yake saman wata qawatacciyar minotti sofa qwaya biyu dake bayan qwatattun Belgium sofas din da aka yiwa yalwataccen parlor din ado masu wani irin design me daukan hankali. Daga bayan Belgium sofas din aka yi wani muhalli na daban da aka zuba minotti sofas guda biyu wanda suke bashi daman kashingida ko miqe qafafunsa a duk sanda yaso. Dogayen qafafunsa na miqe saman sofa din,yayin da night shirt dinsa ke ajiye a gefe,daga shi sai gajeran wandon rigar wanda iyakacinsa cinyoyinsa. Hakan ya bayyana zallar halittar fararen cinyoyinsa dake lullube da baqa sidik din gargasa. Madaidaiciyar Ac ke kadawa cikin dakin,wadda ba lallai yanayin sanyin ya sanya ka fahimci itace ba saboda glass door din dake hannun hagu na falon da yake a bude,tatacciya iska me kyau dake tasowa daga jikin tsirran da aka qawata wajen dasu tana busowa zuwa cikin falon. Tattacciyar iskar data sanya masa kasala da mutuwar jiki,duk karsashin aikin da yakeyi ya soma raguwa. Turo qofar da akayi shi ya sanyashi dauke idanunsa daga karanta saqon da William ya tura masa ta email da suke buqatar ya duba da kyau ya karanta ya kuma sanya hannu. Fes yake ganin fuskarta wadda ke tsaye daga bakin qofar,fuskar data bayyana tsakanin lullubin mayafinta wanda yadan zame baya kadan ya bawa kwantacciyar sumar dake gaban goshinta daman bayyana sosai. Fararen idanunta da suke da wani irin haske ta zube a kansa wani abu na dukan zuciyarta saboda yadda ta sameshi. Ba wani abu da gajeran wandon jikinsa ya suturta sai qasan cibiyarsa zuwa cinyarsa,don bai samu daman qarasawa gwiwarsa bama sam. Ginannen jikin nasa daya samu kulawa ta kowanne fanni,motsa jiki,tsananin tsafta da kuma cima me kyau. Kwantaccen gashin dake cike da qirjinsa shi ya zamewa faffadan qirijinsa tamkar adon baqin abu bisa farin yanki ko farar takarda. Wani irin kwantaccen gashi daya shirya kansa da wani irin siririn layi har zuwa cibiyarsa ya zarce har qasa. Har cikin jikinta taji rudewa sosai,don wani abune da tsahon rayuwarta bata taba gani ba,hakazalika bata taba hasashen zata shigo ta sameshi a haka ba. Cikin zafin nama ta juya da niyyar komawa inda ta fito,don batajin zata iya ci gaba da daurewa kallon wannan halittar tasa. Da nasa salon hanzarin da kuma son qurewa rashin kunyarta tare da qoqarin fuskantar wani abu daga gareta ya dauki remote na qofan ya dannan close,take ta rufe kanta da wata irin gaggawa kamar qiftawar ido. Cak ta tsaya zuciyarta na bugawa sosai,tsoro yanaso ya kamata Amma kuma wannan dakakkiyar zuciyar ta taso mata,taji a ranta cewa idanma ta juya ta fita ta nuna masa ta damu dashi kenan ta kuma damu da wanzuwarsa a haka. Nasa idanun ya janye daga kanta yana hade ransa tsam waje daya. Duk da kallon data masa bai wuce na second biyar ba amma ya fahimci lallai ta qarewa jikinsa kallo. Hannu ya miqa gefansa ya jawo night shirt dinsa ya zura,sai ya koma ya jingina da fuskar minotti sofa din yana ci gaba scrolling saqon yana dubawa. *_DUNIYATA LITTAFIN KUDI NE(PAID BOOK),KAI TSAYE KI TUNTUBI WANNAN NUMBER_* 08187255862 𝐃 𝐔 𝐍 𝐈 𝐘 𝐀 𝐓 𝐀 _Zafafabiyar_ ̶B̶O̶O̶K ̶2 ⱧɄ₲Ʉ₥₳ 𝙋𝘼𝙂𝙀 34 _Daga hassan dan sumra R A yace,daga manzan Allah S A W yace:Duk macen da waliyyai biyu suka aurar da ita ga maza mabanbanta a lokaci guda,to ita din mallakin na farkon ce(wanda aka fara daura mata aure dashi)_ 34 Minti daya biyu uku har zuwa biyar bataji motsin komai ba,wannan ya sanya tayi tsammanin yabar falon ne,don haka ta juyo a hankali tana sake zube idanunta a wajen da yake. Haushi takaici da bacin rai suka hadu suka lullubeta ganin aikinsa yake hankali kwance,sai ta gyara tsaiwarta sosai tana fuskantarsa ganin ya lullube wannan faffadan qirjin nasa,wannan ya dan rage mata kaifin abinda takeji,duk da cewa cinyoyinsa dake a waje nason sakata a razani da tsoro. Rasa ta yadda zatayi calling attention dinsa tayi,sai ta danyi gyaran murya kadan cikin qufula da fusata. Minti guda kaman baisan tana wajen ba kafin ya motsa,ya daga kansa da idanunsa daga kan hasken system din yana zubesu a kanta da wani irin kallo na qurilla. Karo na farko yadda ya tsareta da ido taji kaman yanaso yayi mata nauyi,jajayen lips dinsa hasken fararen qwayar idanunsa wani abu ne da bata taba gani wajen wani d'a namiji ba sai a kansa,akan nasa ma a yau data masa kallo itama nakai tsaye. "Wayoyina nazo karba saboda ina da buqatarsu....... Akwai mutane masu muhimmanci a rayuwata da nake da buqatar na dinga magana dasu" Ta fada tana tsuke girarta da kyau tana kuma tura dan qaramin bakinta gaba wanda sam batasan ma tanayi ba,saboda zuciyarta cike take da haushi. A hankali ya sauke idanunsa zuwa saman qaramin bakin nata data tattara lips dinta duka ta turasu gaba. Wasu irin siraran lips da sai kayi tsammanin jambaki ta shafa musu. Tsigar jikinsa ta zuba kadan saboda bayyanar daya daga cikin abinda ke burgeshi a jikin mace yake kuma lissafin ya sameshi kenan,wato cute lips masu nau'in light pink ko red me haske irin nasa. "A hakar kamar cikakkiyar mace" Ya fada qasan ransa yana jan tsakin da baisan ma ya fito sarari ba. A duk lokacin da zai kalleta sake raina shekarunta yakeyi,hakanan a duk sanda zaya kalletan sai mamaki ya sake cikashi game da yadda ta samu cikakkiyar shaida da certificate din zama KARUWA. shi kam gaba daya ma baisan me yahau kan mazajen dake mu'amala da ita ba,a bisa qa'ida da yanayin halittarsa ta masa yarinta da yawa. Yanason macen daya tabbatar zata iya dauke lalurarsa komai girmanta,ire iren sabreen din guda goma yana ganin yafi qarfinsu nesa ba kusa ba,baima san abinda mazajen da ta dinga tatsewa me suke tsammanin samu haka daga gareta ba da har ta samu tasirin gusar musu da hankali. "Labari kike bani?.....ko tambaya kike?,ko daukan excuse?" Yayi maganar a nutse yana dage mata dukka girarsa guda biyun bayan ya dora qafarsa daya saman daya,ya kuma yi relaxing jikin makarin sofa din. Duk sai ta ji ya muzantata,akanme zai dinga mata tambaya akan abinda ya gama fahimtar inda ta dosa?. Tsaiwarta tadan gyara tanason hana kanta jin nauyin idanuwanta. "Amma dai cikin zamanmu ba sharadin tabamin waya.....wayata sirrina ne,bana tunanin akwai abinda ya shafeka a ciki" Ido ya zuba mata kamar bazaiyi magana ba,yanaso yaci gaba da karantar bayan karatun da yayi mata na binciken da yayi a kanta. Ya fuskanci akwai burbishi da tasirin rashin kunya tattare da ita. Yarinyar da ko saddiq ba sa'anta bane ballanta musaddiq ko farouq.....amma tana da zarrar tsaiwa ta fadi mishi magana yadda takeso. Wannan wani abune da ba wata diya mace data iya fuskantarsa dashi....kai koda dan uwansa namiji yana matuqar shakkar hakan. Uwa uba akwai tasiri na girman kai da rashin tsoro tare da ita,yanaso yaga ya zatayi handling wadannan attitude guda biyun da wadannan shekarun nata?. Kaman zaiyi magana sai wayarsa ta dauki tsuwwa,manhajar da yakanyi amfani da ita wasu lokuta da zata gaya masa cikakken sunan wanda ke kiransa koda bashi da number wayarsa ta karanto masa sunan fareeda Khaleed mustapha. Kusan a tare suka kalli wayar shi da ita,a nutse ya cire hannunsa ya kashe wayar gaba daya bayan yayi rejecting call din,amfanin manhajar kenan ta gaya masa wanda ke kira,basai ya saki aikinsa ya dauka ba ya zamana me kira baida wani muhimmanci har haka,saboda mutum ne shi mai darajta lokaci. Agogo ya kalla sannan a nutse ya maida dubanshi kanta bayan ya sauke qafafunsa duka qasa,abinda ya sanyata sake kame ganinta gudun kada idanun nata su gano mata abinda yafi qarfinta,don ta lura kamar bayajin nauyin zamansa a haka. "Kin tsallake iyakarki,kin shigomin part ba tare da Neman izini ko sallama ba......and kin tsaya kina ban labari akan abinda bai shafeni ba.......wai...." Ya fada yana tsuke fuskarsa sosai gami da maida qafafunsa saman table sabanin dazu dake kan sofa "Meye amfanin zamanki a gidan nan?.. Kina zaton na kawoki ne don na killaceki waje daya kiji dadin rayuwa?,ki samu tsaro kiji dadin ci gaba da qwamushe asusun mutane?,ko na kawoki ne don kizo kicinye min abinci na?,ko kin dauka na daukoki ne don wani abu daban?,thought ma dai nasan ba zaki taba mafarkin wannan shirmen ne wato SO ya sanya na kawoki ba....." Wani radadi takeji yana taba zuciyarta,abu daya da zata iya yabonsa akai takuma san ya qware akai shine baqar magana kamar tsohon mahauci,idaninta da suka fara canza launi takai kansa,ya gyara zamanshi sosai yana hade yatsun hannunsa guri daya yana maida dubansa kanta. "Kina magana akan sharadi yarjejeniya da sauransu......for now ma yakamata kisan me ya shigo dake cikin gidan nan.......Initially don ki gane me ake kira da respect........attitude dinki su koma irin na kowanne mutum.....secondly kuma..........ki maida min dukka kudina da kika debe.....don ban nema kudina saboda mata irinku su mora ba......" Wani kallo harrr ta bishi dashi,sai ya daga dukka girarsa sama "Yes......duk wanda zayaci kudina to yana da cikakkiyar hujjar da zata bashi daman cin in a polite way.......da naso a ranar da kika diba a ranar zan saka a kawomin ke har nan..... " Idanu ta zubawa Kyakkywar fuskarsa yadda yake bayani a nutse hankalinsa kwance. Ashe shi din ma mayen kudi ne?,kallon kitse akewa rogo?. Eh tasan tabbas ta cire kudade masu nauyi da yawan da ita kanta sai data girgiza,amma kuma bata dauka har xai sanya qulafucinsa akan kudin daya tsere musu ba har haka. "Baki da hanyar da zaki biya Muhammad jadda kudinsa?......zan taimakeki tsill dai don kada kiyi prison a banza.........daga yau ya daukeki aikin shara da gyara masa bedroom da kuma wanke masa toilet dinsa......zan biyaki kaman yadda yake biyan kowanni ma'aikaci dame aiki a qasansa.......but.....i will not pay you anything.......zanyi writing down komai har ki kammala biyana" Yakai qarshen maganar gaskiyar abinda yake fada tana fita daga cikin idanunsa. Soma tattare takardunsa yayi "You can go" Ya furta cikin halin ko in kula. A lokacin tana jin kamar ta qarasa gabansa ta amayar masa da dukka abinda ke zuciyarta,tana jin kamar ta isa gabansa ta nuna masa wace real sabreen,amma kuma wani sashe na zuciyarta yana kwabarta tare da gaya mata any mistake idan tayi itace a ciki. "Ya soma cin abincinki shine abinda ya kamata ki damu dashi bawai maganganunsa ba......if kikayi abinda zai sake sanya masa shakkan sakewa da gidan dukka ayyukanki zasu koma baya.... Sisters dinki zasu ci gaba da zama qarqashin hadari" Maganganun da suka fito daga qasan zuciyarta kenan,suka kuma sanyata tsaiwa cak daga takun data fara don matsawa zuwa gareshi. Remote din ya dauka ya bude mata qofar yana ci gaba da abinda yakeyi "Hey" Taji ya sake fada sanda ta sanya qafarta daya a waje,saita dakata ba tare data waiwayo ba "Mind you....banason qazanta,i don't want it,ki kiyaye". Da sassarfa da kuma hanzari ta soma sauka saga stairs din har kamar zata fadi. Kuka ne yakeson qwace mata amma bataso yaji ko ya gani,don ta yiwa kanta alqawari ba zata taba bari yasan lagonta ba. Baqincikinta yadda ya fadi mata dukka maganar da ke ransa,nata zuciyar da ruhi cike maqil da maganganu amma TARKON da take ciki yasa bazaiyuwu ta fiddasu ba. *_Washegari_* Tun shida na safe zuwaira ke kai kawo tsakanin shiyyarsu zuwa ainihin falon da kuma kitchen din. Jin shuru ba alamun tashi sai ta fara aikin gyaran dukka falukan da kuma kitchen din. Duk wani motsi da zataji hankalinta yana kai,tanaso ta samu cikakken bayani akan komai yadda zata zama cikakkiyar informer na maamah. Tanason bata duk kalar bayanan da takeso don tana son ta doke matsayin hajja harira wajen maamah. Ta kowacce fuska da kuma yanayi tanason ta taka matsayin da zata zama aljihun daman maamah a sanda burin maamah ya cika din. Itama tata zuciyar da ruhin cike suke da nata kalar burin da take fatan zuwan ranar wanzuwarsa. Wani irin qarfi ta sanya ta danne zuciyarta ta fito shirya masa breakfast,duk da asara akayi daren jiya na dukka girkin da sukayi,sai tashi tayi tsakiyan dare ta kwashesu ta zuba a inda ta saba zubawa. Yau din cikakkiyar shiga tayi,ta rufe jikinta sosai tunda ta fahimci ba ita kadai bace cikin gidan. Idanunta duka sunyi nauyi saboda kuka da rashin cikakken bacci. A hankali take ratsa falon hankalinta yana qofar kitchen din. "Barka da fitowa ranki shi dade" Taso ta tsorata kadan,don gaba daya ta manta da wata baba zuwaira a gidan. Ta sauke dubanta a kanta sanda zuwaira ke qare mata kallon qwaqwaf. A jiya batayi cikakken bacci ba sai data gama fahimtar inda kowannensu yake kwana ita dashi. A gaban idanunta ta sauko daga samanshi a gaggauce cikin bacin rai ta fada dakinta,abincin dataxo ta kwashe kuma baici ba,a daren itama bata kwanta ba ta sharhantawa maamah komai. "Ya zama dole na matsa mata lamba ta yaudaroshi ya zama a tafin hannunta" Abinda maamah ta furta kenan,tsoron taurin kai irin nasa yana damunta. Tasan halinsa da kafiya akan abinda baida niyya baiyi masa ba......amma zata sake yin amfani da qarfinta a matsayinta na uwa karo na biyu. "Barka kade" Ta amsa mata a taqaice ba tare data sake dubanta ba tayi kitchen "Nace ba,ba abinda za'ayi kuma?" "Babu....kije saina nemeki" Ta amsa mata a taqaice,don kwata kwata batason doguwar magana gaba daya. Da kallo zuwaira ta bita har ta shige kitchen din,sai ta saki murmushi tana ji a ranta ya kamata taci tudu biyu fa......bangaren maamah din da bangaren yarinyar.....abinda ta kwana kenan tana tunani akai,gwara tayi amfani da damarta,ta yadda koda gaba kome ya faru zai zame mata ribar qafa,salon maganar nan da hausawa kance idan tayi ruwa rijiya,idan kuma batayi ba masai. Dukka 4glass stove gas din ta kunna kowanne ta dora abu akai. Da zafi zafinta ta saka 'yar basirarta ta kammale breakfast din cikin taqaitaccen lokaci,ta gyara inda zata gyara ta fara daukan luxury Warmers din tana jerasu saman dining. Cikin ginshira da wani irin tsanaki gami da nutsuwa yake saukowa daga saman stairs din,kunnensa manne da Bluetooth yana amsa waya,lokaci guda kuma yana qoqarin gyara tie dinsa. Hankalinta yayi nisa sosai cikin duniyar tunani,fargaba kuma na sake cikata kamar kullum na kada a sake tafka asara yaqi cin komai kamar kullum,asarar da take sake kusantata da faduwarta da samun matsala a rayuwarta. Tun daga nesan idanunshi suna kanta,duk da baiga fuskarta ba amma ya gane itace. Sai ya dauke dubansa yana haurawa zuwa steps din ya wuce zuwa kitchen. Qamshinsa kadai shi ya ankarar da ita,ta daga kanta tana bin bayansa da kallo gabanta yana wani irin faduwa,cikin mutuwar jiki ta ajjiye spoons din hannunta taja kujera daya tana jiran fitowarsa cike da hope. *_DUNIYATA LITTAFIN KUDI NE(PAID BOOK),KAI TSAYE KI TUNTUBI WANNAN NUMBER_* 08187255862 𝐃 𝐔 𝐍 𝐈 𝐘 𝐀 𝐓 𝐀 _Zafafabiyar_ ̶B̶O̶O̶K ̶2 ⱧɄ₲Ʉ₥₳ 𝙋𝘼𝙂𝙀 35 _Daga abdullahi dan abbas R.A yace,Lokacin da aliyyu R.A ya auri nana fadima,sai manzon Allah S A W yace"ka bata wani abu(a matsayin sadakinta),sai sayyadina Aliyyu yace "ba komai a wajena" Sai manzan Allah S A W yace "ina sulkenka?"_ 35 Coffee ya hadawa kansa,yayi tsaye jikin kitchen cabinet yana kurba a hankali. Kwanakin nan duka baici wani abincin arziqi ba,sai kame kame da cin abincin waje,wanda yasan totally isn't safe musamman ga mutum sannanne irinsa da ta kowacce fuska cikin barazana da qoqarin kawo musu hari ake ta duk wata siririyar kafa da za'a samu dama. Iya lamarin maamah da yarinyar ya isa zama izina a gareshi,abu a cikin gidan.... Amma kuma farautarka akeyi. Sai yaji gaba daya coffee din ya fice masa a kai,yana qaramin tsaki ya ajiye cup din,ya ciri paper towel ya goge lips dinsa duk da ba baci sukayi ba ya fara takawa a nutse yana fita a kitchen din. Sau daya tak ya kalleta ya dauke kansa,ya taka a nutse yana isa gabanta. Tsaiwarsa ta sanyata daga kanta,akwai inches tsakaninsu amma tana jin kamar ba wani gap daya rage musu. Idanunsa saman lips din nan nata da suke very smooth,ba digon komai akai sai ainihin color dinsa. Smart key na qofarsa ya dora saman table din,ya kuma harbasa gabanta. Ya motsa labbansa zaice wani abu wayarsa ta fara fidda wani tattausan ring me kama da sarewa,irin ring din da zai iya haifarwa da mutum karyewar zuciya musamman ga masu karyayyiyar zuciyar. Fareeda Khaleed mustapha sunan wanda ke yunqurin samun sadarwa dashi kenan aka sanar mishi. Maimaita kiran sunan me kiran wayar ta soma yi kamar ba zata dakata ba. Saman kunnuwanta sunan ya sauka,irin sunan da taji a wancan daren. Iska ya furzar daga bakinsa yana sauke numfashi,sannan yana qaramin tsaki gami da ciro wayar da wani dan zafin nama yana yanke kiran ya jefata aljihun yana sake sakin tsakin. Baki ta tabe qasa qasa tana kauda fuskarta wani sashen,can qasan zuciyarta kuwa gulma take,tasan za'a rina.....koda dukka jikinta kunnuwa ne ba zata taba yarda mutum kamar muhammad jadda bashi da kowa ba.....mutum kamar muhammad jadda baida ajiyayyun 'yammata da yake debe kewarsa dasu ba......ba zata yiwa kanta qarya ba,idan tace mummuna ne ko bai hadu ba tasan tabbas wannan din gundumemiyar qarya ce ta zabgawa kanta......to kuwa tasan zai wahala a rasashi da wasu halaye da sukayi kama da wannan. A iya rayuwarta.....a iya mazan data hadu dasu harda wadanda basu kaishi bama,masu kudi sosai matasa masu jini a jika,taga dabi'u kala daban daban da halayen da bata ma tsammaci ganinsu ba,yaga yadda matan aurensu suke ba komai ba a wajensu......taga irin qalubalen da shuke fuskanta a tattare dasu....matasan cikinsu harma da masu yawaitar shekaru,wannan abun ya sake cire mata sha'awar abubuwan nan guda biyu a ranta SOYAYYA da kuma AURE. Gadai guda daya nan ya cimmata,saidai tana da yaqinin ba zata bari yayi galaba a kanta ba,yayin da take bawa kanta tabbacin tafi qarfin wata soyayya taci galaba a kanta,don idan ka dauke soyayyar qannenta bata taba tsintar kanta cikin soyayyar komai ba,wannan shine yake sake bata yaqini tabbaci da nutsuwan ba zata taba yin soyayya ba....saidai ita a sota (Nace uhmmm....maji ma gani wai an binne tsohuwa da ranta). Idanunsa ya maida saman fuskarta,a nutse ya fara magana kamar wanda ya hada jini da gidan sarauta. "You can start your work today.......but......ya kamata ki sani,nasan komai da yake every single room......sannan nasan place dinshi,so do your own business......kiyi iya abinda akace kiyi" Daga haka sai ya juya a nutse don sauka a wajen,saidai kuma muryar da yaji tana gaidashi ya sanyashi tsaiwa yana juyawa wajen. Zuwaira ce a durqushe a wajen,da yanayin da yake tabbatar masa ba yanzu yanzu ta shigo ba. Sunkuyar da kanta tayi sanda ya zube mata kaifafan idanun nan nasa,yayi mata wani irin kwarjini da bata taba ganinsa idanun kowanne mahaluki ba sai a kansa. Wannan kwarjinin nasa ya sanya suke qauracew waje duk sanda ya shigo gaida maamah. Sosai goshinta ya soma tsatstsafo da gumi,tana ganin kamar a iya kallonsa kadai zai iya bankado komai ya kuma fallasashi. "Who are you?" Yayi tambayar kai tsaye ba wani wasa ko sassauci a muryarsa,abinda ya sanya zuwaira ta ida rudewa,ga turancin daya jefeta dashi wanda ya saka a duhu "Eh....na'ammmm.....eh" "Wacece ke?" Ya maida mata tambayar da hausa. Caraf ta kama maganar tasa "Nice zuwaira.....zuwaira ce,me aikin da hajiya maamah ta aiko don taya uwargida sabgogi da hidimomin gida". Ta qarashe fada tana daddafe hannuwanta a qasa,saboda ji tayi kamar zata fadi daga tsugunnen. Hannayensa kawai ya zube a aljihun wandonsa yana ci gaba da kallonta,yana kuma son ganin fuskarta sosai. Duk wani daya rabi maamah yana da nashi question mark din a wajensa.....duk wani wanda maamah zatayi qoqarin hada connection tsakaninsa dashi baida aminci ko nutsuwa kwata kwata dashi,don haka yake sake shawarwarin qarawa musaddiq kwanakin zamansa a qasar da ya aikeshi ba tare da wani qwaqwaran dalili ko kuma buqatar hakan ba. Hannayensa nasa ya sauke ya soma takawa yana sauka daga wajen,zuwa sannan qiris ya ragewa zuwaira ta saki fitsari a wando. "Kada na sake ganin gilmawarki cikin gidan nan indai ina nan......duk ranar kuma da kikayi sake hakan ya faru.....ki fara hada kayanki na barin gidan nan....basai nace ba" "In sha Allahu ranka ya dade,tuba nake" Ta fada dukka jikinta yana rawa. Daga ita har sabreen ba wanda yacewa da dan uwansa komai. Kusan minti biyar da fitarsa sannan ta tattara qarfinta ta miqe tana sake hawa steps din dining da sabreen ke zaune akai. Fuskarta qunshe da munafukin murmushin nan ta soma gaidata "Barka da asuba ranki ya dade.....ashe har kin gama aikin?,ba zaki jira nazo ba?,hidimar ai sai tayi miki yawa,da sai na rage miki ai.....iyaka idan na gama abincin ki bada kalar maganin da za'a zuba a ciki......kedin abar tausayi ce ranki ya dade,kullum addu'ata da fatana ki kubuta daga hannun hajiya mariya lafiya" Zuwaira tayi maganar cikin matuqar sanyin muryar.....tsantsar alhini da kuma nuna damuwa. Tunda zuwaira ke maganganun nan a jejjere sabreen bata daga kai ta kalleta ba sai da tazo gabar qarshen maganar tata. Kalmar tausayi data furta a maganar nata yaja hankalin sabreen ya kuma tsaye mata a rai. Sosai ta zubawa zuwaira idanu tana son tantance gaskiyar abinda ta fada,saidai kuma abun mamaki haka kawai sai taji ta kasa gamsuwa da ita. Boyayyen numfashi ta sauke,sannan ta tattara hankalinta a kanta tana hade ranta tsaf "Wannan duka ba huruminki bane.....kiyi abinda ya cancanci kiyi kawai" Sai ta miqe daga saman kujerar tana niyyar tafiya. Da sauri zuwairan ba tare da ta ji ciwon tsaidata a wata iyaka da tayi ba tace "To ranki ya dade abincin fa?,yauma saidai a zubda?" "Idan kina da buqatar ci kya iya ci ai" Ta amsa mata da gatse tana sauka daga step din idanunta yana sauka kan laila dake shigowa parlor din. Sanye take da robber gown wadda tabi kowanne shape na jikinta ta lafe mata. Fuskar nan fes da kwalliya zaka rantse ba safiya bane ba. Ba komai a kanta sai wani qaramin bandana da bai rufe komai a gashin kanta ba. Wani mahaukacin tashin qamshi jikinta keyi,wanda turaren turare ne na musamman da aka tanada saboda wani mutum na daban. Duk da fuska ko kuma jikinta ba wata kwalliya.....amma haka kawai ta fusgi hankalinta. Sassanyan kyan nan nata da baya buqatar kwalliya ko wani abu makamancin haka yana nan shimgide saman fuskarta. Haka kawai taji ta muzanta duk da kwalliyar dake jikinta,amma duk da haka sai taji ta raina kanta. Tashin farko wasu kalmomi na hajja suka dawo mata fes cikin kwanya suka qara mata azama da qwarin gwiwa. Muhammad jadda kawai take da buqatar gani,don haka taci gaba da shigowa falon tana jin izza tare da fatan ko yaya ta gwadawa sabreen wani abu da zai sosa ranta. Kallo daya ta yiwa lailan ta watsar da ganinta a wajen,taci gaba da wucewa ciki ba tare data damu da kallon qurillar da laila ke mata ba. Ita sam bata ma dauketa a sunan damuwarta ba,damuwarta ta tsaya ne kan yadda yake neman maidata boyi boyin qarfi da yaji. Ta share masa sassa ta hada da wankin bandakinsa dama underwears dinsa,tana jin koda sama da qasa zasu hade ba zatayi wannan aikin ba. Lumshe idanunta tayi tana qara jin takaici yana cikata. Bashi da masaniyar hatta da girkin da take masa dole ce ta sanya take masa ba?,har wani qyashi da baqinciki ke rufeta gami da kasalar bacin rai duk sanda ta tsinci kanta dumu dumu a kitchen tana hidimar dafa masa abinci. Dakinta kawai ta wuce bayan ta saqale masa key dinsa jikin qofarsa,tana fatan ya dawo ya samu sassansa da muqullansa a inda ya barsu. Dining din laila ta wuce kai tsaye tana wani taku kai kace itace matar gidan,ranta ya cika maqil da kishi da hassadar sabreen din. Ko daga nesa ka hangosu sabreen din ta fita quruciya.......amma miskilancin yarinyar da shegen girman kanta mamaki yake bata. Bata taba mata kallo biyu ba....kai zata ma iya rantsewa sau daya ta mata nutsasten kallon cikin idanu Randa taso blocking mata hanya. So take ko yaya taga wutar kishinta a idanunta,to amma kullum suka hadu tana yin kamar babu aka kawo gidan aka ajiye ba dan adam ba. "Ma aka dafa?" Ta tambayi zuwaira Kai tsaye tana latsa wayarta sanda zuwaira ta kusa gama kwashe warmers din. "Sai yanzu Allah yayimin tashi,don haka saiki jira na gama da aikin matar gidan tukunna" Zuwaira ta gaya mata gatse gatse gami da satar idanunta ta gasa mata harara. Kullum ta tuna warning da kuma jan kunnenta akan ta yiwa yarinyar biyayya da hajiya mariya da hajja uwar yarinyar suka mata akan tabi yarinyar sau da qafa bama matar gidan ba.....sai taji kamar ta zabge yarinyar da mari. *_DUNIYATA LITTAFIN KUDI NE(PAID BOOK),KAI TSAYE KI TUNTUBI WANNAN NUMBER_* 08187255862 𝐃 𝐔 𝐍 𝐈 𝐘 𝐀 𝐓 𝐀 _Zafafabiyar_ ̶B̶O̶O̶K ̶2 ⱧɄ₲Ʉ₥₳ 𝙋𝘼𝙂𝙀 36 _An karbo daga abu hurairah Allah ya qara yarda dashi yace,manzon Allah S A W yace,idan miji ya kira matarsa zuwa shimfida taqi zuwa,mala'iku zasuyita la'antarta har gari ya waye_ *_qarqashin wannan hadisin akwai qarin haske,idan a wannan qin da tayi kuma ta samu ciki koda ta rasu wajen haihuwa wasu malamai suna ganin bata samu wannan shahadar da mace me naquda ke samu ba idan ta rasu_* 36 "Ki gaggauta da Allah.... Am starving,ko ki bani wannan da kike debewa in fara dashi" "Sannu akuya......" Zuwaira ta fada a ranta,amma a fili saita ajiye mata warmer din tana cewa "Zaki iya ci mana.....amma kafin kicin ki fara sanarwa tsohuwarki gudun maida laifi a kaina" Ta fada dadan zafin rai. Haka kawai sai laila tasha jinin jikinta,don haka ta miqe tana sauka daga wajen "Fresh nakeso.....kada ki wuce minti talatin" Bata ma iya amsa mata ba ta dauke ragowar warmer din tana wucewa kitchen din gami da jan tsaki qasa qasa. Tafiyar minti arba'in da shida ta sadashi da mansion House din alhaji hamza kibiya. A qofar tafkeken gate din dake qara nuna alfarmar dake cikin gidan motocin suka tsaya bisa umarninsa,don yanaso ne ya gaida anni ya fito......ya kuma haida maamah din sannan ya wuce office din. Akwai cushewar ayyuka sosai yau din bisa schedule din da saddiq dinsa na yau da saddiq ya tura masa tun jiya da dare,wannan ya sanyashi fita da wuri. Wani irin qarin investors suketa samu a dukka kamfanoninsu,duk da yana yin komai bisa kula don ya tabbatar akwai mutanen dake bibiye dashi,kuma nasararsa a wancan lokacin yayi imanin ta tarwatsa musu dukka shirinsu..... Faduwarsu kuwa da shurunsu yayi amannar bawai suna nufin komai ya wuce bane. Gidane dake cike da tsari,da kuma kusan duk wanda yake gidan bisa tsari da sanin ya kamata yake zaune. Kowa yasan aikinsa,tun daga kan security guards da sauran masu aiki na cikin gida dama farfajiyar gidan,hakanan bayin Allah da suke daukan nauyi dake wani sashe daban na cikin gidan me kama da qaramin estate kowa bisa tsari da sanin ya kamata yake. Duk girman gidan ko.ina fes yake da wani irin tsafta da qamshi. Ya zuqi qamshin har cikin hunhunsa sanda yake zama saman sofas na qaramin falon anni da mutanen da suke mafi kusanci da ita ne kadai ke iya haurowa har nan. Ba abinda ke saukar masa da nutsuwa kasala gami da tayar masa da wnai Tsunammen feelings irin qamshi. Duk sonshi da qamshin wannan ya sanyashi haqura dashi kan bedsheets da duvet nashi da pillow,wanda muddin ya kwanta akai da qamshi irin wannan to zai wahala bai kwana cikin wahala ba,ko kuma ya tashi da mafarkin da zai wajabta masa wanka kafin yakai ga sallar asuba. Normally yanaso kowanne kusurwa na inda zaiyi mu'amala dashi ya zama kaman haka,sai ya lumshe idonsa kafin ya budesu sanda yaji sallamar anni. Da dogon hijabin nan nata har qasa ta shigo wanda ke alamta masa sallar walaha take ya tasota. A wajenta ya koyi sallar walaha,tun yana yi yana fashi batabi jininsa ba har takai ya saba,ko a ina yake,kome kuma yake yi sai ya katseshi yayi,saidai idan abubuwan sunsha kansa ko sunfi qarfinsa ba yadda zaiyi. Fuskarta shimfide da kararramammen murmushin nan nata ta qarasa shigowa,tayi bismillaha tana zama saman kujerar abinda ya sanyashi zamowa daga samanta yana gaidata. "Tashi ka koma ka zauna" Tace dashi don ba kasafai yake iya zama saman kujerar ba idan suna kai ko ita ko abbansu,harma da maamah din kanta. Kai ya girgiza yana tanqwashe qafafunsa saman carpet kamar qaramin yaro "Nan ma ya isa anni.....akwai kunun tsamiya?" Kai tadan daga tana dubansa. Batayi tsammanin zai qara tambayar abinci ba sam sam daga wajenta,don kuwa a yanzun magidanci sunansa,saidai kuma ta masa uzuri,don tunda akayi auren bai taba neman komai ba,don haka tace dashi "Akwai.....kasan dole ne kullum sai an yiwa abbanku.....har yanzu gargajiya taqi barinku,bari nasa a kawo maka" Ta fada da murmushi. Shima tsadajjen murmushin nan da kusan annin tafi kowa ganinsa a duniya ya sake "Anni akwai abubuwa masu muhimmanci me tarin yawa a gero,inda mutane sunsan meye gero anni da kusan duka mun koma cinsa". Murmushi ta kuma yi tana miqewa gaba daya "Gaskiya mana naga kun qulla kyakkyawar alaqa da fura.....nikam wannan traditional doctor din naka ya sake canzaka gaba daya" Murmushi kawai ya saki,shi kansa ya sani kalar cimarsa ba iri daya bace data kowa,sau tari a wani taro ko a sanda ya buqaci cin abinci da baqinsa na Africa ko nan Nigerian,sukan cika da mamaki idan sunga kalar abincin da yake ci. Da kanta annin ta shiryo komai saman tray,harda qarin lafiyayyen qosai da kuma farfesun kan rago da yasha kayan qamshi tafarnuwa da wadatacciyar albasa. Akwai abinda takeson ta karanta a tattare dashi a fakaice a matsayinta na uwa bawai kai tsaye ba. Tun daga ranar da amna ta gaya mata zaunuwar zuwaira a gidan ko sau daya bata taba hutawa da tunani ba. Ta kasa aminta hakanan ta kasa gamsuwa. Fu'ad dan maamah ne halak malak,duniya ma ta shaida hakan,saidai tana jin bai kyautu tabar mata rayuwarsa ba,rayuwar da aka fafata aka sha fama kafin fara daidaituwar komai a cikinta. Allah shine ya raya muhammad fu'ad din,amma kuma itace sila,tasha fama qwarai da gaske,faman da har batason tunawa,faman da shine ya zama silar shaquwa tsakaninsu me yawan gaske. Har batason tuna wahalar da tasha dashi kafin cire shi daga depression daya samu kansa a ciki. Tana shigowa ya miqe,bai barta ta qaraso ba ya isketa a hanya ya karba tray din ya qaraso dashi. Sanda yake shan kunun a nutse yana kuma cin qosan tana zaune a gabansa tana karantarsa,tana jin zuciyarta na matsewa,ta kuma damu tayi masa maganar dake qasan ranta,duk da haka tayi jarumtar sanda ya kammala sannan a tsanake tace dashi. "Muhammadu...." "Na'am anni" Ya amsa mata a nutse yana jin wata nutsuwa da qoshi na musamman yana ratsa cikinsa. "Nace anya yarinyar nan basai an taimaka mata da qarin masu aiki ba?,gidan nan sai nakega ko masu aiki nawa aka zuba masa yana buqatarsu ko don sauqaqawa matar gidan,duk da yake kai baka fiya son mu'amalar masu aiki ba cikin sha'aninka". Murmushi kadan ya saki,baisan wanda a duniya ya sanshi sosai ya kuma karanceshi tas sama da anni ba. "Kiyi duk yadda ya dace anni......" Ya bata amsa cikin girmamawar data sake sanyata ta jishi a ranta sosai. *_DUNIYATA LITTAFIN KUDI NE(PAID BOOK),KAI TSAYE KI TUNTUBI WANNAN NUMBER_* 08187255862 𝐃 𝐔 𝐍 𝐈 𝐘 𝐀 𝐓 𝐀 _Zafafabiyar_ ̶B̶O̶O̶K ̶2 ⱧɄ₲Ʉ₥₳ 𝙋𝘼𝙂𝙀 37 _Daga ibn juhaim bin haris RA(wannan sunan sahabin annabi ne😄),yace:Manzan Allah S A W yace "da me wucewa ta gaban me sallah yasan abinda yake kansa na sabo,tabbas da ya tsaya(ya jira me sallahn ya gama)tsahon gwargwadon shekara arba'in shine yafi masa alkhairi akan ya wuce ta gabansa_ _Bukhari da muslim ne suka rawaito_ 37 "Da ina tunanin na tura mata ma'u da maigidanta malam ibrahim.......zataji dadin zama da ma'u sosai.....ina kyautata zaton haka,malam ibrahim kuwa koda kana da ma'aikata da sauransu zakaji dadin zama dashi in sha Allah". "Anni ki zartar da komai da kike ganin ya kamata......ba buqatar sai kin gayamin anni" Ya sake fada har a zuciyarsa yana jin annin ta isa ta zartar da komai din. Kai ta jinjina tana dan murmushi,har qasan ranta tana jin dadin yadda ya bata girma da kuma dama,duk da cewa tasan cewa abune me wahala ya musanta akan duk abinda tace din. Har bakin parlor na biyu tayi masa tattaki,bakin ta fal cike da addu'ar data zame mata dole,kowacce rana dukkaninsu su hudun basa kaucewa samun kyakkyawar addu'arta da bata gajiya da binsu da ita. Qafarta daya saman daya take zaue cikin qawataccen parlor din nata da idan ka kirashi kai taaye da aljannar duniya bakayi kuskure ba,duk da ita a nata ganin sam har yanzu bai kai matsayin da take buri tsari da kuma mafarkin yakai ba. Dukkan hankalinta ta baiwa zuwaira dake zayyane mata jawaban da muhimmancinsu a wajenta ya wuce kimar komai data mallaka a duniya. Jawabin dake da wani irin kima tamkar ta zinare a idanunta. Duk da bayanan ba abinda suke haifar mata sai wani irin tashin hankali. ba irin bayanan da take buqatar taji kenan ba.....amma duk da haka suna da muhimmanci a wajenta,don sune zasu zame mata tamkar tsani kuma fitilar da zata haska mata matakalar da zata taka zuwa matakin gaba. "Amma fa tana qoqarin ganin ta aiwatar da aikinta......saidai ban hangi wata shaquwa soyayya ko kusanci da junansu ba ko kadan" "Wannan kuma aikinta ne......ita kuma ya kamata ace ta fara samar da wannan dangantakar a tsakaninsu......a nan gazawar tata ta fito.....ta kowacce hanya ya kamata ta yaudari zuciyarsa har ya aminta da ita ya miqa mata wuya.......aikinki yana kyau zuwaira,ina buqatar magana da ita yanzun nan kafin na yiwa tufkar hanci tun daga tushiya" "Yanzun zan sadaki da ita uwar dakina" Zuwaira ta fada cikin karsashi gami da jin dadin lambar yabon data samu. Batasan adadin sau nawa ta duba agogo ba tana zaman jira da dakon kiran zuwaira. Qaguwar da tayi ya hanata jira zuwairan ta kirata ta maida kiran zuwa wayarta. Ya shiga a daidai kuwa,sanda take rusune daga bakin bedroom din sabreen tana qoqarin fahimtar da ita amfanin kiran. "Ina jinki kamar d'iyata ko jikata....ki daure ki saurareta,taqi kadan zai rage ku rabu in sha Allah". Duk bata gamsu da matar ba,duk da batajin nutsuwa da matar ko kalamanta,amma a ciki akwai abinda takejin gaskiya ne,a ciki akwai abinda takejin da gaske ya kusa tabbata din TAQI KADAN YA RAGE SU RABU. Hannu ta saka ta karbi wayar,sai ta tura qofar bedroom din ta rufe ta koma ciki. Tana takawa cikin idanunta suna kan fuskar wayar,yau din a matuqar tunzure take,so batason wani magana da zata sake hasala hali da kuma yanayin da take ciki. Gaban madubinta taja stool ta zauna,sannan ta kunna wayar ta sakata a hands free ta dorata saman madubin,sannan kuma a hankali ta maida idanunta saman fuskarta kamar me kallon maamah din zaune a gabanta. "Ina jinki" Ta furta a nutse yana goye hannuwanta a qirjinta. "Ina fata kina cikin lafiya da kuma aminci qarqashin kulawar d'ana?" Tayi maganar a nutse tana son kamo bakin zaren ainihin maganarsu. Kamar ba zata amsa mata ba,sai ta daga idanunta daga kallon dogayen yatsunta da gaba daya lallen da akayi mata na aure ya fice tas,tamkar ma ba'a taba digawa yatsunta lalle ba,ta maida oily eyes din nata cikin madubin daya bayyanar da fuskarta dinnan me shimfidadden kyau dake dauke yau din da wani irin kwantaccen fushi. Zubawa fuskar tata idanu tayi kamar yau ta fara ganin kanta da kanta,iya kallon kawai yana motsa zuciyarta gami da tuna mata a karan kanta wacece sabreen,wani sashe na zuciyarta ya motsa yayi aikin daya jima baiyi ba,taji wani abu ya darsu a zuciyarta wanda ta jima tana yunqurin daddago dashi amma yana komawa "Ki ajiye wannan a gefe.....yaya jikin huda?" Tayi mata tambayar da take kwana da ita tana tashi ba tare da tasan waye zata yiwa ita ya kuma basu cikikkiyar amsar da take buqata ba. "Jikin huda?.....alhamdulillah......saidai ban da tabbacin yadda ya kamata ya kasance". A hankali ta lumshe idonta tana son yiwa amsar tambayar tata fashin baqi. Bugun zuciyarta yana son ninka gudunsa saboda samun mabanbantan amsoshi daga mabanbantan lunguna da saquna na zuciyartata wadanda basuyi daidai da fatanta dama abinda takeso taji ba. "Mu ajiye wannan......zan dan yaba miki game da yadd kike qoqarin ciyar dashi abinda muka baki,saidai har yanzu kin gaza cimma manufar abinda kikeyi din......caring kulawa.....ba wata halitta da batasan kulawa.....dole ki fara samun zuciyarsa kafin ki samu cikinsa da jikinsa....." ".......ba wannan cikin jarjejeniyarmu.......wai shin..kina zaton ina da buqatar zuciyarsa?,ko ina da buqatar hanyar da zata sadar dani ga shiga zuciyarsa?". Tayi maganar kanta tsaye da wani irin tsauri,saboda zafi da a yau zuciyarta keyi mata,tana jin kamar wani abu me kama da gajiya da kuma fara jin takura yana mintsinin zuciyarta. Murmushi me sauti maamah din ta saki tana gyara zamanta "Bana fatan ki samu zama ko shiga zuciyarsa na dindindin,a taqaicema dai....banda yanayi irin na lalura banjin kinkai quality din da zan baki license na shiga zuciyar mutum me tsada,namiji irin muhammadu ba.....amma karki manta,dole ne ki sadaukar masa da komai don isa ga burinmu.....idan nace komai ina nufin komai da komai fa,na zabeki ne saboda ina da tsammanin zaki iya bada komai don cikar muradina.....koda kuwa jikinki ne...." "Ya isa!" Ta furta a tsawace saboda jin maganar tata ta fara shallake guri,uwa uba tana neman fin qarfin kanta. "Kibi a hankali......a yanzun duk da ban mallakeshi ba,amma zakisha mamakin abinda zai biyo baya idan har na shaida masa matarsa tana min shouting tana kuma dagamin murya....." Zafin radadin maganarta ta farko bata saketa ba,don haka bata maida hankali sosai akan maganarta ta biyu ba. Burinta shine ta furzar mata da abinda yake ranta,tana jin kamar takai maqurar da zasu dinga wasan tamaula da ita tsakanin ita da d'anta. "Zanci gaba da ci dashi kaman yadda iya abinda yake zayyane kenan a bisa yarjejeniyarmu......daga hakan banajin zan qara akan komai.....faduwarki ko nasararki ya ta'allaqa ne da yadda na samu tabbacin lafiyar qannena" Daga haka ta katse wayar kawai tana ajeta a gefe. Taso tayi tariyar maganganun da sukayi da maamah din,amma a yau sai taji gaba daya bata da buqatar tuna komai.....kawai tana jin ba zata iya ci gaba da zamowa kamar tamaula tsakanin su ba. Wani irin confidence takeji,saita miqe tana komawa bakin qofar da zummar ajewa zuwaira wayarta,ta dauka duk sanda ta dawo,don ko haduwa da ita bata sonyi. Ga mamakinta a tsaye ta sameta a bakin qofar kamar wadda aka bawa gadinta. Wani kallo ta jefeta dashi tana jin sam matar bata mata ba "Ba wani abu da ake buqata?" Ta fada da sauri bayan ta karbi wayar ganin sabreen din na zummar shigewa ciki "Babu" Ta bata amsa a taqaice tana maida qofarta ta kulle. Yadda yau yarinyar ke amsa mata magana a tsaitsaye sai takejin kamar akwai abinda ta taka,akwai abinda ya bata confidence a kanta. Ci gaba tayi da juya wayar a hannunta tunaninta yana yin nisa gami da rarrabuwa kashi kashi. Wani tunani ya kutso mata cikin kwanyarta "Me yasa ba zaki murza kambunki ba?,ki gwada qarfin iko da mulkinki ba har akan fu'ad din?" Wani sashen na zuciyarta ya bata shawara. Shuru tayi tana sauraren daya bangaren tare da juyar maganar cikin kwanyarta. Kai ta gyada tana bawa kanta tabbacin tabbas wannan din zaiyi aiki.....koda baiyi diki dari bisa dari ba to akwai yiwuwar samuwar galaba. Tana qoqarin kiransa ta shaida masa tana buqatar ganinsa sallamarsa ta mamayeta. Tana amsa sallamar farinciki na cika zuciyarta yadda Allah ya dubeta ya jefo mata shi,saidai a saman fuskarta ba haka bane. Ranta yana hade,hakanan ta boye duk farincikinta don tanason ko meye zata gaya masa ya daukeshi da muhimmanci. Sai daya iso gabanta ya zame yana gaidata ta hanyar tsugunawa saman qafafunta. Bayan ya gama gaidata din shuru ya biyo baya,a nutse yace "Ba komai da ake buqata?,ba wani matsala?" Yayi tambayar data zame masa wajib duk sanda yazo gaidatan don qoqarin sauke haqqin Allah da yakejin ya zama wajibi ya sauke din. Kai ta girgiza fuskarta a daure. "Ba abind nake buqata.....amma matsala dai akwaita". Daidaita tsugunnonsa yayi kafin ya zame ya zauna sosai a gabanta. Duk sanda tayi wannan yanayin kota furta magana makamanciyar wannan zai wahala idan ba wani aikin bane zaya zameshi. Idanunsa yadan lumshe gami da budesu duka lokaci guda cikin qoqarin hadiye fargabarsa,yana tunkarar qalubale komai girmansa.....gaagwarmaya komai wahala da kuma taurinta,amma har yanzu zuciyarsa baya iya jure wadannan halayen da maamah din,dabi'unta suna kassarashi,ya kasa sabawa,baisan me yasa ba,ko don ita dinn wata jigo ce da abubuwanta ke tafiya ba yadda ya kamata ace sun tafi ba?. "Wacce matsala ce?,me yake faruwa?" Ya tambayeta a nutse. *_DUNIYATA LITTAFIN KUDI NE(PAID BOOK),KAI TSAYE KI TUNTUBI WANNAN NUMBER_* 08187255862 𝐃 𝐔 𝐍 𝐈 𝐘 𝐀 𝐓 𝐀 _Zafafabiyar_ ̶B̶O̶O̶K ̶2 ⱧɄ₲Ʉ₥₳ 𝙋𝘼𝙂𝙀 38 _Daga abi sa'eed RA yace:manzan Allah S A W yace; "idan dayanku yazo masallaci,ya duba takalminsa,idan akwai qazanta ya shareta ya kawar da ita daga jiki,yayi sallah da takalminsa_ *_halal ne sallah da takalmi a qafa,na haramci a ciki muddin ba najasa a jiki_* 38 "Muhammadu" Ta kirashi da ainihin sunansa,ba tare kuma data bari ya amsa ba ta dora "Nikam bansan a rayuwa akwai wani abu da yafi haihuwarku da nayi muhimmanci ba" Idanu ya zuba mata yana jin tamkar ya tashi ya fita da gudu ya tserewa maganganunta,don yasan zai wahala ba kamar kullum bane,dora masa nauyi da mas'uliyyar da zai gaza dauka kota masa tauri. Kai ya girgiza,ya buda baki zai magana ta sake danneshi da kalamanta "Bansan wanne irin rashin muhimmanci nake dashi a rayuwarku ba da har zan zartar da hukunci cikin rayuwarka,nace kum ga alfarma ko abinda nakeso kayimin ka gaza yi din,ace har yanzu maganganun ameenatu da umarninta yana zama gaba da nawa?" Ta qarashe maganar tana jin dacin haka sosai har cikin zuciyarta. Batasan wanne tozarci ma ya kamata ameenatu ta fuskanta ba aduk sanda haqanta ya cimma ruwa,har yanzu idan tayi hasashen abinda zata saka ta fuskanta sai taga wannan hukuncin yayi kadan. Sam baya qaunar ta dinga sanyo maganar anni cikin maganganu da ayyukansu,don bazai iya tuna sanda anni ita tayi magana a kanta ba indai ba alkhairi ba. "Muhammadu.......yanzu ni da hannuna na baka amanar yarinyar mutane......na roqeka ka mu'amalanceta kamar kowanne miji da mata.......ka kyautata mata ma faranta mata,ka jata a jiki amma haka ga gagara?,ka kasa cikamin wannan alfarmar da zata bayya a irin kima da martabata a idon yarinyar?". Qasa yayi da kansa,shi maganar ma nauyi tayi masa sosai akai. Ta wani gefen kuma ranshi da zuciyarsa suma motsa. Yanzu har taurin kan yarinyar da tsaurin idonta yakai ace ta kawo ma maamah qararsa?,har da maganganu irin wadannan marasa dadin ji?. Sai data gama dukkan wani fada baice komai ba,har sai da tayi shuru sannan yace "Kiyi haquri,in sha Allah za'a sake yin qoqarin gyarawa da canzawa". Ya furta a taqaice. Har cikin ranta yadda ya amsa mata haka a sauqaqe ya faranta mata sosai "To Allah yayi albarka" Ta fadi kalmar da bazaice when last da yaji ta fada ba. Muryarsa a sanyaye ya amsa mata,sannan ya miqe yana mata sallama yana fita daga falon. Tun kafin ya qaraso Jordan ya wangale masa qofa,da wani irin zafi ya isa ya shige motar Jordan ya maida murfin motar ya rufe. Suit dinsa na sama ya fara ballewa yana zareta daga jikinsa saboda wani irin zafi da yakeji tun daga zuciyarsa har cikin fuskarsa. Iske me qarfi ya fesar daga bakinsa bayan ya zuqi wata "Wanne abune meqarfi da girma a tsakaninsu bayan wannan?" Ya jefawa kansa da kansa tambayar yana motsa labbansa. "Ita ta shiga jikin maamah ko maamah ce ta shiga jikinta?" Ya sake maimaita tambayar da ba wanda zai iya bashi amsarta. Yanzun har matsayinta da girmanta wajen maamah yakai ya samu sanyawar albarkar maamah din saboda dalilinta?,wanne aiki take mata haka me faranta rai bayan abinda yake suspecting?. Tunanin daya rakashi kenan har cikin office dinsa,ya kuma wuni yana tayashi zama,duk kuwa da uban tarin ayyukan daya samu suna jiransa. Duba documents da sanya hannu cikin wasu takardun,wasu takardun suna da buqatar hankalinsa da nutsuwarsa kafin yakai ga sanya hannu,da qyar ya hada hankalinsa bayan sallar la'asar ya soma duba wasun,bayan ya yiwa kansa matsayar matakin da zai dauka. Komawa tayi ta sake kwanciya bayan sallar la'asar din,tana lissafin nan da awa daya koda rabi zata shiga kitchen saboda shi.....saboda mutumin da ba ganin girma qima ko martaba sam sam tsakaninsu. Idanunta ta runtse,a yau tana jin wani zafi zafi na yadda maamah ta bautar da ita. Batasan me yake tilastata lallai saita yi sai kuma ta cika muradin maamah din ba. Tsaki taja tana bude idanun nata,sai suka fada saman gift din da anni ta bata ranar da suka je. Dan murmushi ta saki qasan zuciyarta,matar ta kwanta mata a rai,tana da wani irin calmness me taba zuciya nutsuwa da kuma wani irin kwarjini. Tashi tayi tsam ta daukosu ta dawo ta zauna saman abun sallarta data tashi ta soma budewa tana tuna fuskar matar da takejin kamar ta taba ganinta a wani wajen kafin yanzu. Littafin farko ta dauka daya qunshi addu'o'i akan kowanne abu,harkokinmu na yau da kullum. Shafin farko ta bude,sai ta dinga tuna zamanin da ummensu ke raye,Lokacin da take tsaye a kansu kai da fata,ba batun fashin islamiyya ko wani abu da yayi kama da wannan. A duk dare itace malamarsu,zata zauna a tsakiyarsu saita tabbatar kowanne karatunsa ya zaunar masa akai,musamman karatun addini da a nan tafi qarfi,na bokon tafi jiran abbansu idan ya dawo,musamman idan ya zamana itace da girki,idan ba ita bace dole saita dauki uzuri an bata lokaci. Hannu tasa ta shafi addu'ar farko da sam ta mantata cikin rayuwarta,ummensu itace ta fara koya mata ita tana kuma iya tuna lokacin har yanzu,sai ta tashi ta koma saman sofa ta zame kadan tana bin addu'o'in daya bayan daya tana dubawa suna kuma sake tuno mata da kansu. Sosai takejin dadin karatun,don ya debe mata kewa me yawan gaske. Babu zato daga saman kanta din,daidai wata kyakkyawar qaramin luxury stand taji qaraurawa tana kadawa. Zubawa wajen ido tayi,wata mulmulalliyar na'ura ce da take zubi da telephone. Tunawa tayi amna ta taba dagawa tayi kira zuwa parlor sanda sukazo,sai a sannan ta tuna na'urar sadarwa ce da aka shiryata duka gidan da kuma tsakanin dakunan gidan har zuwa Kutchen,wannan ya bata qwarin gwiwar saka hannu ta daga ta sanya a kunnenta. "Ranki ya dade......malamarki ce tazo,sabuwar malamar da yallabai ya daukar Miki saboda karatun yamma". "Malama kuma?" Ta tambayi kanta da kanta cikin tsananin mamaki tana son tuna yaushe sukayi wannan maganar da shi?. "Duk cikin salon da zai miki mugunta ya cusguna miki ne kaman yadda ya dauki alwashi". Ido ta lumshe tana budesu sannan a nutse tace mata "Ki sallameta zuwaira......ko kuma ta jira wanda ya tattagota din" Daga nan ta kife wayar tana komawa ta zauna qirjinta a quntace. Wannan abun da yayi me yake nufi kenan?,ita din jahila ce?,ko batasan komai ba saishi zai sanya a karanta mata?. Wannan tunanin ya tsaidata,sai data gama baqin ran da bacin ran sabon salon wulaqanta mutum daya bullo dashi......hakanan ba don taso ba ta miqe tana wucewa kitchen. Tana shiga zuwaira na fadowa,sai ta waiwayo tana kallonta. Cikin jikinta wani abu ya bata,ta yaya duk wani motsinta zuwairan kamar tana biye dashi ne? "Ranki ya dade dame za'a taimaka miki dashi?" A nutse ta juya kawai ta fara aikin gabanta,kamar ba zata amsa mata ba sai kuma ta tura mata lettuce da cabbage carrot da peas tace ta gyara ta yanka mata. Zaman kurame kawai sukeyi cikin kitchen din,zuwaira nata satar kallonta tana son ta dan tabota da magana don ta gina alaqar sabo a tsakaninsu amma bataga wannan fuskar ba sam "Tashin hankali" Zuwairan ta fada qasa qasa,daga ita har mijin haka fuskokinsu suke kamar na shanu? Ta tambayi kanta,ita dai har yanzu bata taba ganin fara'a ko dariyar dayansu ba. Sai da suka kammala komai sannan ta fidda magungunan zata cakuda kaman yadda ta saba. Ta bude murfin ta karkata gorar,sai kuma ta tsaya cak. A hankali ta daga idanunta ta zubesu akan zuwaira data tsaida komai tana son tabbatar da zubawar. Karon farko da cikin jikinta taji kamar nauyin idanuwan wani yana kallonta zatayi abinda bashi ya dace ace tayi ba akan wani,duk kuwa da tasan jirgi daya shine ya debo zuwaira da ainihin me kwangilar,amma a yau saita ji wani nauyi. "Zaki iya bani space?" Ta jefa mata tambayar taba dinke girarta sosai fiye da dazu. "Au to....to ranki ya dade" Ta fada adan daburce sannan ta juya tana fita a kitchen din. Haushi ya sanyata kwarara da yawa,idan komai ya qare ai a huta,taga ta inda zata tuhumeta kuma,sai taja tsaki tana jefa roban a shara sannan ta juya ta fice tana baiwa zuwaira dake falo umarnin taje ta jerasu,sai ta wuce kai tsaye zuwa dakinta. Itama din a gaggauce ta shiryasu tana kallon kayan,baki ta tabe,tana jin haushin yadda lafiyayyen abinci irin haka yake salwanta,ga nasu iyalan can cikin yunwa da buqatar abincin da baikai wannan bama,amma akan mutum daya anata asarar lafiyayyen abinci irin wannan. Hankalinta ta maido jikinta da sauri,saita juya tana barin falon cikin son kiyaye dokarsa da tsoron kada ya dawo ya sameta a wajen kamar yadda ya shardanta mata. K'arfe Tara da wasu mintuna motocinsa suka tsaya a farfajiyar gidan bisa halastaccen parking da kowanne driver na kowacce mota ya qware akai. A nan harabar gidan ya barsu ya wuce ciki shi dame sunan malam,wanda iyakarsa qofar parlor din farko ya juya shima yana komawa cikin guard da security na gidan dake qoqarin tabbatar da tsaro da lafiyar kowacce mota kafin masu tafiya su wuce a sake tabbatar da tsaron gidan sannan a maidashi a rufe kaman yadda yake,shida da fita kuma sai da izinin masu gidan. A hankali yake ratsa falon farko zuwa na biyu kafin ya isa stairs dinsa. A gajiye yake don duk sanda yayi dare irin haka a company to tabbas cinkoson aiki ya riqeshi ne. Tun daga nesa yana taka stairs din ya hangi maqullin maqale jikin qofar,ya isa a hankali ya sanya hannu ya cire sannan ya tura qofar parlor din. A nan zarginsa ya tabbata,mug din da yayi amfani dashi a daren jiya yana zaune abinsa dirshan saman side table din,yayin da dish din da yayi amfani shima dashi yake zaune saman dining abinsa hankali kwance. *_DUNIYATA LITTAFIN KUDI NE(PAID BOOK),KAI TSAYE KI TUNTUBI WANNAN NUMBER_* 08187255862 39 _Daga abu hurairah Allah ya qara yarda dashi yace:mazan Allah S A W ya ambaci ranar juma'a,yana cewa "A CIKINTA KAWAI WANI LOKACI,BA WANI BAWA MUSULMI DA ZAI RUSKETA YANA ME TSAIWA YANA SALLAH YANA ROQON ALLAH WANI ABU FACE SAI ALLAH YA BASHI ABINDA YA ROQA DIN". sai manzon Allah yayi nuni da hannunsa na qanqantar lokacin (ma'ana baida tsaho,Allah yasa muna cikin wadanda zamu yita ruskarshi)_ Wani bacin rai ne karon farko ya sauko masa,ba abinda ya dawo masa akai sai abinda ya faru a dazu. Yadda maamah ta fitittike tana jaddada masa yadda takeso ya mu'amalanceta ko ya kula da ita,amma ko kusa ko alama shi baiga alamun tasan darajar kalmar aure ba koda kuwa auren 'yar tsana aka daura,ballantana shi data deba kudaden da ranta keso,karamci kuma ya sanya suka qara mata da wasu abubuwan da shi kansa baisan me su anni suka kashe ba. Duka sai yaji abun bai masa ba bai kuma zauna masa akai ba,ya kamata ya qara bata lesson. Yana takawa zuwa bedroom din nasa yana watsar da kayan hannunsa,kama daga socks takalminsa suit briefcase dinsa da sauran tarkacen daya shigo dasu. Wani budewa hancinsa yakeyi yana tsukewa saboda bacin rai,ya tsani raini ya kuma fahimci halinta ne,ya tsani rashin kunya ya kuma karanci dabi'arta ne. Bai dakata ba sai da yayi wanka,ya hadawa kansa fruit salad a gurguje yasha,sannan ya zauna yana jawo wayar sadarwar yana kiran number dakin nata. Ta gama komai tuntuni,ta kuma jima da kwanciyar saidai baccin da baizo ba. Tayi mamakin jin kiran,saita sanya hannu ta dauka tana tunanin zuwaira ce,ko meye kuma ya faru a daren nan oho?. Muryarsa taji sabanin muryar zuwaira da tayi tunanin itace. Har tsakiyar kanta sautin muryar ta sauka mata da wani irin zuzzurfan amo "Hello" Ya fada yana qoqarin hadiye bacin ran dake taso masa. Matsar da kan wayar tayi daga kunnenta da zummar sauke wayar,kaman yasan abinda take shirin yi ta tsinci muryarsa cikin zafi yana magana "Kika kuskura kika sauken waya....zakisha mamaki na". Tsauri umarnin nasa yayi mata,saita samu kanta da gaza ajiye wayar. Sau tari tana mamakin yadda yake cin galaba a kanta haka da sauri,umarninsa yake saurin ratsata,wani abu guda daya da ta raina akan kowanne d'a namiji. Bata taba zato ko tunanin akwai wani lokaci da zaizo da wani namiji zai iya juyata ko ya canzata daga abinda yayi mata daidai cikin rayuwarta ba,sai ga abun yana tafiya cikin rashin zato bare tsammani.....kamar a cikin duniyar mafarkinta. Ci gaba tayi da riqon wayar ba tare data ce komai ba,haka daga nasa bangaren bataji ya sake furta komai ba. Kusan minti daya wayar na a riqe a hannunta,sakannin kuma suna ci gaba da motsawa. Kaman daga cikin wayar taji an murda qofa an kuma budeta. Sauyin yanayin qamshin daya soma mata sallama ne ya shaida mata tabbas an bude mata qofa,ba kuma cikin wayar bane a zahiri ne. Tana kwance ne rub da ciki,don haka ta waiwaya kadan don tabbatarwa da idanunta. Muhammad jadda ne,tsaye daga baki qofar dakin yana riqe da handle din,daure da lallausan farin towel wanda ke dauke da tambarin VERSACE baro baro a jiki. Gaba daya towel din ya daurashi ne daga iya qugunsa,ya kuma sauka sosai zuwa mararsa,abinda ya bata damar ganin full ginannen jikin nan dake cike da lallausar gargasa data kwanta tayi luf luf. Fadin kafadunsa ya sanya bata ko iya hangen qofa,sai yau ta sake fahimtar GIANT ne na gaske,da murjajjen jiki da kuma ginannun tsokokin damtse dana qirjin wato(muscles). Wani mahaukacin faduwa gabanta yayi,a yau taga abinda bata gani ba a wancan ranar data sameshi a parlor dinsa.....ko don yau din a tsaye yake da dukka tsahonsa da kuma wadataccen haske a dakin nata?. Duk yadda take da kafiya da taurin rai sai data gaza ci gaba da kallonsa,wani irin tsoro ya kamata wanda ya tilasta mata maida kanta ta kwantar saman pillow tana baiwa qofar dakin baya,wato qeyarta ke kallon qofar kenan. Gabanta ya sake yankewa ya fadi sanda taji ya maida qofar ya rufe gami da murxa key,ta fidda idanunta dukka biyun waje tanason yin hasahen abinda zai iya faruwa da ita,saidai bata gama wannan ba taji an sanya hannu an birkitota gaba daya,sai gata ta koma rigingine a maimakon rub da ciki da take a dazu. Gaba daya ya zame mata rumfa saman kanta,tamkar me barazanar hanata ganin komai na dakin sai wannan mudadden jikin nasa. Da hanzari ta sanya tafukan hannayenta guda biyu da zummar tureshi saboda yadda yake neman hade space din dake tsakaninsu,amma ko gezau kamar ma ba wani hannu daya sauka a jikinsa. Bai bata second chance ba ya kama hannuwan nata ya matse cikin hannunsa guda daya. Qoqarin qwatar kanta sosai ta farayi tana tureshi,amma baiko motsa ba,yana riqe da hannuwanta gaba daya yana kuma ci gaba da zube mata idanunsan nan "Ka sakeni......ka cikamin hannu" Ta fada sanda ta fahimci ko kusa ko alama bata da qarfin da zata iya amsar kanta a hannunsa. Ta cikin idanunta ya fahimci laushi tayi,hakanan qarfinta ne ya fara qarewa. Bayajin zai qyaleta haka sai ya bata mummunar barazanar da ba zata qara kai qararshi wani guri ba. Duk dabaya tunanin wani tsoro me yawa a tattare da itan duba da ita din WACECE?. Ba wani sabon abu bane a wajenta cudanya da maza,duk da maza suna suka tara kamar yadda mata suma suka tara suna. "Inajin a matse kike a sauke miki jarabar da take damunki ko?,wannan ya sanya ba kunya cikin idanunki kika je kina kai qara a inda kike tunanin za'a sanyani sexual affairs dake ko?". Duf wuta ta dauke mata,daga iya kalmar sex data shigo maganar ta tabbatar lallai babbar magana aka baro. Yaushe takai qararsa?,kuma gurin waye?,me tace tana da buqata?,duka wadannan tambayoyin sune suka soma mata yawo saman kai,kuma inda tana da hali tana da buqatar amsarsu,saidai a yadda komai yake a hautsine bata jin tana da tattararriyar nutsuwar nemansa da wadannan amsoshin. Tana aje wannan tunanin yana sakin hannun nata,ya miqa hannu da wani irin zafin nama zuwa Coller din rigarta,wadda tsaurin riqon da yayi mata ya bawa bottom daya damar tsinkewa fit. Fitarsa sai ya zamana kamar ya hada da fitar nutsuwa daga gangar jikinta,wani tashin hankali ya rufto mata har kala biyu. Na farko yadda yayi kusa da ita da towel din da kadan ya rage marabarsa da tsirara,don babu abunda ya lullube illa mararsa zuwa gwiwarsa,na biyu kuma fitar maballin rigarta sai ya tuna mata waccan ranar a kitchen. Ranar da har yau idan ta dauki rigar data sanya a ranar sai taji qamshin wannan mayataccen turaren nasa,abinda ya sanyata kenan tayi adabo da rigar duk kuwa yadda take sonta. Saboda duk sanda ta sakata haka yadda abin ya faru zai yita dawowa kanta,hakanan kuma zatayita tuna yadda ya azabtar mata da lips haushinsa yayita kai komo kenan a ranta har sai ta raba kanta da ita. Matse hannunta yayi yana saukar dashi daga gaban rigar don so yake ya tsinke maballi na biyu,kafin ta iya komai har ya samu nasarar yin hakan,ya kuma wuce zuwa maballi na gaba,abinda ya sakata saka hannuwanta dukka biyun ta cukuikuye gaban rigar,cikin fushi kuma taci gaba da magana "Don't touch me.......ka daina tabani mana.... Wai mene haka?!". Ta qarasa fadi sanda ya tattara hannuwanta da zummar turesu,cikin rashin sa'a hannuwan nasa suka samu nasarar sauka daidai saman tudun qirjinta wanda ke tsaye car babu bra. Sabonta ne idan zata kwanta dukka saita ciresu,don tana jin kamar suna hanata cikakken bacci. Daga shi har ita ba wanda baiji kaman an yarfa masa wuta a jikinsa ba,yayin dashi ya hada wani azababben shock daya ratsa jininsa da wani irin mahaukacin gudu ya aike saqo qwaqwalwarsa ya kuma dawo da saqon yana rabawa zuwa sassan jikinsa gaba daya. Taji komai har cikin jinin jikinta,sai taji kamar an zare mata dukka wata laka tata da wani irin firgici da tsoro bakinta ya furta "Please......don Allah ka bari" Kalaman nata na qarshe ya fito da zirarowar hawaye zuwa saman kuncinta. Duk yadda yaso ya zarce da tsoratata gami da gigitata cikin mugunta sai yaji ya kasa,haka ya sake mata rigar yana dauke idanunsa daga kanta ba tare daya bari sun sauka a inda take boyewar ba tamkar sulalewar ruwan kalkashi a tafukan hannun mutum. Zuciyarsa ta cika da wani irin mahaukacin mamaki......daga ina wannan weakness din ya taho?,ya tambayi kansa da kansa can qasar zuciyarsa. Bai taba niyyatar zai dauki mataki akan wani abu ba tare daya qarasa aiwatar da qudurinsa ba,bai taba jin rauni akan duk wani abu daya sanya a gaba ba sai akan wannan dan qaramin aikin. Tattare jikinta tayi waje daya tana neman hanyar sauka daga saman gadon,amma sai ya sanya gwiwarsa ya take gefan rigar,ya waiwayo a nutse ya zube mata idanunsan nan masu dauke da wani kakkaifan maganadisu,wanda duk yadda sukakai ga haske sun surka launi a yau din. "Kina zaton zan hada jiki dake ko?,over my dead body......duk randa zan hada jiki dake ki sanya a ranki ranar mutuwarki ne kawai yazo,don zan niqaki da kyau kaman yadda engine ke niqa tsaba ya koma gari....." Yatsunsa ya murza saman fuskarta sannan yace "Sharadi guda biyu ne zan baki idan kin kiyaye shikenan.....na farko....kada ki kuskura ki sake kaiwa maamah qarata koda akan meye kuwa....ban hanaki kaiwa anni ba idan kinga zaki iya fine.....sharadi.na biyu duk randa na sake miki umarnin yin wani abu kika watsar kina daukan kanki wata tsiya.....zakiga abinda zai biyo baya,sai na sanya an sako Michael yayi dambu da namanki,ki tashi kizo ki gyaran sassa.....ki kuma samu note pad ki rubuta day one don lissafinmu yafi tafiya daidai" Yana kaiwa nan yaja jikinsa yana sauka daga gadon,ya kuma fara takawa hankali kwance yana fita daga dakin. Da sassarfa yake haurawa saman cikin tuhumar kansa da kansa. Baisan kanshi da kasawa ko gazawa ba,ya akayi ya kasa bata mummunan punishment yadda ya kamata?. Koda ya tsaya gaban mirror na toilet din,sai ya dinga jin haushin kansa da kansa. Baisan wani weakness nasa ko kadan ba......amma sai ya samu kansa yana tsoron kada fa wannan ya zama shine weakness dinsa?. *_DUNIYATA LITTAFIN KUDI NE(PAID BOOK),KAI TSAYE KI TUNTUBI WANNAN NUMBER_* 08187255862 𝐃 𝐔 𝐍 𝐈 𝐘 𝐀 𝐓 𝐀 _Zafafabiyar_ ̶B̶O̶O̶K ̶2 ⱧɄ₲Ʉ₥₳ 𝙋𝘼𝙂𝙀 40 _Daga sumrah dan jundub RA,yace manzon Allah S A W ya kasance yana nemawa mumunai maza da mata gafara a kowacce juma'a_ _harda ni dake da kikazo a wannan zamanin kin shiga ciki,LALLAI HASARA DA TABEWA TA TABBATA GA DUK RUHIN DA BAISON ANNABI,ALLAH KA DAUKI RUYUKANMU RUHINMU YANA CIKE DA MATSANANCIN SONSA S A W_ ________________________________ Moroccon cotton jallab ya saka ta maza maroon color me gajeran hannu,wadda aka yiwa ado da gold din zarurruka masu kauri. Har hantar cikinta sai data kada sanda taji fitowarsa zuwa falon,amma ta dake bata nuna ba,tana duqe tana goge stand tv lokaci lokaci tana goge 'yan hawayen daketa qoqarin lallai sai sun sake karya mata zuciya. Kai tsaye ya wuce saman minotti sofa dinsa yana lumshe idanunsa,wata azababbiyar kasala nason saukar masa. Dole yana buqatar wani abu da zaiyi awakening dinsa for some hours don yana da aiki. "Ke..." Ya kirata idanunsa suna lumshewa kadan. Kiran ya mata ciwo,amma kuma dole ta nuna tasan da ita yake maganar. "Bring me some coffee" Ya furta yana dauke idonshi a kanta ya lumshesu don kaucewa kallonta. Ajiye duster din hannunta tayi qirjinta na mata wata suya,ta fara takawa don isa qofar da zata saukar da ita daga saman "Hey.....ina zaki?" Ya furta da rashin qwarin murya. Sai kuma ya mata nuni da nasa kitchen din da idanunsa,kai tsaye ta gane me yake nufi,ta kuma canza akalar tafiyar tata zuwa can din. Tayita dube dube da tsoron kada ta tabo wani abun duba da yanayin machine da utensils din dake kitchen din daya sake shan bamban dana qasa nesa ba kusa ba. Da qyar ta samu ta kammala,duk da bata da guarantee din yayi ko baiyi ba,don itadai ba damunta yayi ba,koda ya dameta ma ba irin wannan bane.....nasun irin nasun ne wato daidai matsayinsu yaku bayi. Saman tea tray ta hado da cups. Ta qasan idanu cikin lumsassun idanunsa yake kallonta sanda take nufoshi da wani irin kallon da zaka rantse da Allah bacci yakeyi. Yana qoqarin binciken kansa me yasa yaketa tunawa da abinda ya faru?,amma ya rasa dalili,haushin kansa sosai yakeji a yanzun,yana ganin kamar wannan hanyar ta sanya tsoro a zuciyarta bazatayi aiki ba.....zata iya dasa masa matsalar da zata gagari gangar jikinsa watan watarana. Yadda jikinta yayi laushi sosai yake karanta,yana mamakin macen data saba mu'amalantar maza kala daban daban me ya sanyata jikinta yayi laushi don ya mata wani qaramin riqo da bai taka kara ya karya ba?. "Kana murzata ne ta hanyar da ba haka su suke mata ba,da ta irin tasu hanyar ce qila ba abinda zai sanya jikinta laushi" Wani sashe na zuciyarsa ya bashi amsa. A gabansa ta ajiye tana jin inama zata samu wata dama ta zuba masa wannan abun cikin tea dinsa?,qila cikin kwanaki uku ta samu nasarar da zata cika aikinta,ta tattara tabar wannan DUNIYAR tasu ta koma tata ainihin duniyar. "Serve me" Ya fada da murya can qasa. Sake baci ranta yayi,gaba daya a hankali yana son canzata ta koma 'yar aikinsa kenan kome?. Tsugunnawa tayi a nutse ta soma zuba masan tana qoqarin danne zuciyarta amma ta kasa jin relief. A sanda parlor din ya dauki shuru,wayarsa da tafi kusa da ita ta soma kuka alamun shigowar kira. Kallo daya ta yiwa wayar ta dauke kanta,yarinyar kullum ce dai wato fareeda khaleed mustapha. Qaramar tsuka taja,ita ta sani zaa rina,mutum kamar muhammad jadda ace yana zaune lafiya bisa kyawawan dabi'u?,ai ta qalubalanci wannan. Banda akwai wata gurbatacciyar alaqa me zai dinga shigo da kiranta cikin wayarsa a kowanne dare?,a daidai lokaci irin wannan da mafi yawan lokuta yake kebancewa shi kadai?. Tana miqa masa coffee din yana daukan wayar yana kallon screen din ransa yana baci,ya dauke dubansa daga kan fuskar wayar da yakeji kamar ya bugata da bango saboda yadda tsananin nacin fareeda ya soma shallake hankalinsa,ya aje dubansa akan fuskarta dake a dinke sosai. "Fara sha kafin ki bani" Yace da ita a taqaice. Duban rashin fahimta tayi masa,sai ya kafeta da idanu kafin yace "Do you think am a fool?,kina zaton zan karba nasha any how?....." Ya qarasa maganar yana daidaita zamanshi sannan ya tura mata teatray din "Take a sip first" Sai data ja numfashi sosai ta aikawa hunhunta sannan ta samu zuciyarta taci gaba da aiki yadda ya dace,me yake nufi data fara sha?,ta tambayi kanta. "Kada ki barwa kanki qofar zargi" Wata zuciyar ta shawarceta. A nutse ta dauka mug din ta kurba kadan sannan ta ajiye masa,zata motsa yace "Hang on for a bit" Ya fadi cikin halin shariya yana maida hankalinsa kuma kan fareeda tare da tunanin ta inda zai bullo mata. Ambassador yana da kima da mutunci a idanunsa,musamman daya kasance babba harda furfura a fuskarshi,saidai fareeda tana crossing line da yawa da baya bari a crossing masa shi. "What's bothering you?" Ya fadi adan fusace,yayin data narke marya Kamar qanqanuwar yarinya "Kaineee" Labbansa duka ya cusa cikin bakinsa yana qoqarin hadiye takaicin data bashi. Sai ya sauke idonsa akan sabreen wadda baisan ta soma barin wajen ba sai a sannan. "Where to?" Ya jefa mata tambayar data tabbata yanason jin inda zata ne. Ita ba zata tsaya tana jinsa yana hirarshi da matan banzanshi ba,ba damuwarta bane ya yanke dukan abinda yake ganin ya dace da rayuwarsa.....amma ita kuma ba wanda zai tilastata yin abinda batayi niyya ba......wannan din dabi'arta ne da ba canzawa. Sai data yi qaramin yaqi da zuciyarta sannan ta iya lanqwasa harshenta ta sarrafashi tana fadin "Dare yayi inaso na kwanta" "Idan kin gama you can go" Ya fada cikin halin ko in kula yana katse kiran fareeda itama gami da sanyata a DND mode sannan yaja coffee dinsa ya soma kurba. Sassa ne na alfarma dake da yalwa wadatar kayan alatu dana qarau wadanda ke buqatar a gogesu,wannan shi ya sake bata mata lokaci ya kuma dauketa har kusan sha biyu na dare abinda ya bata mamaki samunsa sa tayi dungurgur ya sanya system a gaba ya zuba mata idanunsa yana sarrafata,wanda motsin takunta ya sanyashi rage mata haske sosai har baka ganin abinda ke allon. Baki ta tabe ta qarasa,zuciyarta na ayyana nata waye ma yasan abinda yakeyi tsakiyar darennan. "You are free" Ya amsa mata ba tare daya waiwayota ba,sai ta fara nufar qofar a ran ta tana fadin "Shi mugun mutum ba kasafai bacci dama ya fiya damunsa ba". Gyaran yayi masa sosai,don yafi qawatar dashi fiye da coffee din,don sam bai masa dadi ba irin yadda yakeso ya kasance ba. Jallab din jikinsa ya zare ya wuce toilet da zummar daura alwalar kwanciya bacci. ★Duk a kasalance take kowanne aiki a yau,tun daga safiya zuwa daren da take kammala girkin daren. Sai takejin wani irin qosawa,gaba daya ta fara gajiya da komai. Tunda take wannan shine karon farko data aboci kitchen safe da dare da zummar dora sanwar girki. Kamar ko yaushe bayan ta kammala abincin,ta taka a hankali tana nufar inda ta boye akwatin. Ta jawo ta miqa hannu ta fito dashi sannan ta bude. Kayan cikin ta fara fitowa dasu kaman yadda ta saba,daya bayan daya kuma ta soma zubasu saman abincin ta cakude dasu. Yau daya sai ta tsaya kawai tana kallon abincin,wani irin rashin dadi takejin zuciyarta tana mata a yau din,a kasalance ta maida kayan ta kuma rufe ta maidasu ma'ajiyarsu sannan ta dawo ta soma daukansu zuwa dining don yau kwata kwata ma bata bari zuwaira ta shigo mata ba. Batason doguwar magana,hakanan batason sanya idanu da wannan shegen binbinin kallon da take binta dashi a kowanne daqiqa. Dab da zata isa dining din saita dinga ji kamar qamshinsa. Batasan ya akayi ba.....amma tun daga waccan ranar ta haddace wannan nataccen qamshin turaren nasa da har yanzu yake maqale jikin rigunanta guda biyu. Sosai takejin qamshin,to amma ta raba idanunta ko ina cikin parlor din bata ga wani alamun shigowarsa ko shigowar wani ba. Agogo ta sake kalla sanda take ajiye warmer din,mintuna kadan ya rage ayi sallar magariba.....wannan lokacin kuwa ba lokacin dawowarsa gida bane,don qarfi da yaji ta haddace lokacin dawowar tasa saboda yadda ta aza dukka damuwarta akan cikar burinta na yaci abincin. Watsar da tunanin tayi,taci gaba da shirya komai ta kammala,ta tsaya kawai tana kallon yadda komai yake jere saman dining din. "Inama ace yau daya burina ya samu ya cika?" Ta furta qasan ranta duk da tana jin wani sashe na zuciyarta kaman yana qyamatar hakan ya faru,sai kuma ta juya tana nufar hallway din da zai sadata da dakin. Dab da zata shige laila ta murda pivot door din tana shigowa falon tayi kwalliya sosai cikin wani silk material da aka tsarawa dinkin daya dace da shape din jikinta sosai. Red ne colour dinsa wannan ya sanya farar fatarta data samu gyara da pills na qara fari da allurai na qara hips da sauransu ya sake qawata shigar tata. Kome takeyi tana da cikakken goyon bayan hajja wadda a kullum burinta ta fita daban,ta kuma zama daban din ta kowacce hanya cikin mata. Idanu suka hada,sai sabreen din ta dauke idonta kamar kullum,ta kuma taka a nutsenta tana wuceta,tana jin bata da wani lokaci nata sam sam. Da idanu ta raka sabreen da wani irin kallo na qurilla,allurar kishi tana tsikararta,tana tambayar kanta da wanne irin products haka take amfani masu tsananin qarfi?. Tana ji ana cewa kowanne dan adam tara yake bai cika goma ba.....to amma ita sai take ganin tamkar a halittar sabreen goma take cif cif!. Tsaki taja tana maida dubanta kan dining din. A yunwace ta shigo,ta samu zuwaira kuma bata nan,tabbacin a yau kenan saita shigo da kanta neman abinda zataci. *_DUNIYATA LITTAFIN KUDI NE(PAID BOOK),KAI TSAYE KI TUNTUBI WANNAN NUMBER_* 08187255862 𝐃 𝐔 𝐍 𝐈 𝐘 𝐀 𝐓 𝐀 _Zafafabiyar_ ̶B̶O̶O̶K ̶2 ⱧɄ₲Ʉ₥₳ 𝙋𝘼𝙂𝙀 41 _Daga nana aisha RA tace,manzan Allah S A W yace: "anayin wanka akan abubuwa guda biyar,janaba....da wankan juma'a...da idan anyi qaho,da wankan mamaci(mutum ya yiwa gawa wanka)_ __________________________ Matsawa taci gaba dayi zuwa wajen dining din,tana cike da haushin yadda a kullum ake jigilar qawata wajen da warmers na alfarma wadanda suke bata tabbacin abinci ne lafiyayye.....to amma kullum idan ta tuna maganar da hajja ta gaya mata akan abincin sai ta maida qwalamarta bisa tilas. Asali ita din mutum ce da ba kasafai ta fiya bawa irin wadannan abubuwan muhimmanci ba. Hasalima tana ganin idan ba dominka aka shirya abu ba bazai taba tasiri a kanka ba. A nutse ta isa wajen,ta kuma jawo warmer din farko ta soma budeta,budewar da ya qara adadin yunwar da takeji taji kuma bata da wata hanya illa ta toshe yunwar dake sakadar mata hanji kamar bata taba cin komai ba. Yau gajiya takeji sosai a jikinta,wannan ya sanya data idar da sallah isha'i wanda duka zama tayi a wajen bayan magariba sai data yi isha din sannan ta tashi. Wannan Dabi'arta ce qwaya daya da har yanzu bata rabu da gangar jikinta ba,burbushin raino da tarbiyyar ummensu,bata wasa da sallah sam koda bayan gushewar ummen,kuma ita kanta ta hori 'yan uwanta sosai akai (Ko hori yaranku da sallah.....tana da matuqar tasiri wajen hana bawa sabon Allah da kuma gyara halinsa,kamar yadda Allah ya fada cikin qur'aninsa me girma,tabbas sallah tana hana alfasha da munkari,Allah ya bamu dacewa ameen summa ameen). Tana shirin shiga wankan saita samu kanta da maimaita addu'o'in data karanta a littafin da anni ta bata wanda shi ya qara sanyata jin dadin zaman. Tana nanata addu'o'in suna tuna mata da zamanin da suke qananu......lokacin da ummee ke korasu makarantar allo ranakun weekend,ita hadiyya da sameeha. Qaramin murmushi ya kubce mata,tadan girgiza kai tana jin kewar lokacin quruciyar tata,tana jin inama tana da ikon dawo da wancan lokacin,ashe ba abinda yakai zamanin quruciya dadi. Pyjamas ta saka baqaqe gaba daya da suka sake haska mata fatarta,sai ta dora qaramin farin Malaysian hijab saman kanta bayan ta nannade gashinta a tsakiyar kanta cikin ponytail holder,hakan ya sanya kan yadan tashi kadan kamar tayi acuci maza na. Fararen flip flops ta zurawa fara tas din qafarta,wadda duk wani lalle ya fita a jiki,sai tsantsar haske daga qara da gogewa kamar jini zaiyi tsartuwa. Hankalinsa na rarrabe akan wayarsa sanda yake qarasowa cikin falon. Daidai lokacin da laila ke saukowa daga dining din sai ya zamana mutum na farko da idanunta suka fada a kai. Cak ta tsaya ana zare duk wani noti na jikinta,wannan shine karon farko data taba gaba da gaba da muhammad jadda,kusan duka a baki ko cikin magazines da news paper take ganinsa. Duk yadda tasha fasaltashi a zahirinsa ya wuce nan,wani irin ingarman namiji da a iya tafiyarsa kadai ta hangi izzarsa da kuma cikar isarsa. Kaman a jikinsa yaji ana kallonsa,wannan dalilin ya sanya daga idanunsa yana duban sashen da yaji jikinsa yafi rinjaye. Suna hada idanu gaba daya kwarjininsa ya mata wani irin mamaya data gaza riqe kanta,duk wata zarra da jin kai da takeji tana dashi a matsayinta na diya mace ya sulale yayi nasa waje. Yadda ya kafeta da idanunsan nan masu qunshe da wani sirri sai taji komai yana kwance mata "Barka da dare" Tayi namijin qoqarin furtawa bakinta yana son hardewa "Yauwa" Kawai ya amsa mata dashi. "Nice laila....'yar gidan hajja.....hajja harira ta maamah" Tayi bayanin a nata zaton hakan zai burgeshi ko kuma ya sake bata matsayi na musamman a matsayinta na 'yar aminiyar mahaifiyarsa. Fuska yadan yamutsa kadan yana fahimtar inda ta dosa. "Yayi kyau.....ban fadi muku banson kowa around us ba idan ina gida?" Yayi maganar fuskarsa na wadace da wani irin daurewa kamar baisan sunan wani abu waishi dariya ba,don dama da bacin rai ya sauko. Kasaqe tayi tana mamaki,tabbas zuwaira ta shaida mata,amma ko a sannan kallon banza ta watsa mata ta wuce dakinta,don tana ganin ita ta wuce wannan dokar tayi aiki a kanta. Tana jin kanta tamkar ita din halastacciyar 'yar gidan ce,don haka bata ma wani tsaya amfani da dokar ba bare ta kiyayeta. Tana shigowa a duk sanda taso tayi abinda takeso ta fita,saidai da yake dukkaninsu ba ma'abocin zaman falon bane kowa sabgar gabansa yake shi yasa ba wanda ta taba karo dashi a cikinsu. "Get out of my sight......and kada ki sake bari mu hadu" Ya fada cike da zallar umarni ba tare kuma daya kalli sashen da take ba yaci gaba da tafiya kansa tsaye zuwa dining din. Ajiye wayoyinsa yayi bayan ya gama abinda yake,ya maida hankalinsa ga abincin yana dubansa. Yau zai kawo qarshen duka wannan drama din ya ayyana hakan a ransa,daidai sanda take fitowa daga parlor din zuwa ainihin falon da yake ciki. Kai tsaye dama idanunta kan dining din suka fada,don ya zame mata wani aiki na daban kiyaye waye a wajen da kuma duba waiko ya zauna cin abincin?. Bataso yadda tashin farko suka hada idanu ba don zaya dauka ne kawai kallonshi takeyi,take tata izzar itama ta motsa,ta dauke kai sosai tana takawa zuwa qofar kitchen. "Hey.....com here" Ya fada da matsakaiciyar murya. Tanason gwada masa tsiwar amma tana tsoron abinda zai biyo baya,dole ta dawo din fuskarta shimfide da kalar nata miskilancin. "Serve me" Ya fada cikin basarwa yana bude wayarsa. Cak ta tsaya,tana jin kamar kunnuwanta ne suke jiye mata ba daidai ba. Ta zuba masa abincin fa ya buqata?,ta tambayi kanta tana neman qarin haske. "Zuba abincin nace" Ya sake maimaita mata ba tare daya dubeta ba. Wani irin abu taji ya tsargawa sassan jikinta. Ta dade tana fatan zuwan wannan ranar,ta dauka duk sanda taxo din zata kasance mutum da tafi kowa murna a duniya,amma kuma sabanin murnar mutuwar jiki taji. Matsawa tayi sosai gaban table din,ta ware qananun luxury table mat din ta sake shimfidasu,sannan ya zari plate da bowl ta soma zuba komai tsaka tsakin quantity sannan ta jera masa a gabansa. Wayar ya ajiye a gefansa,ya miqa hannu da kanshi ya ciro spoons guda biyu ya saka cikin abincin sannan ya dubeta "Oya.... Let's eat together" Ya furta yana matso da drinks din da aka aje a wajen duk da ba abun shansa bane sam sam duk wani drink da company ta sarrafa. Ba shiri ta bude idanunta a kansa,ji tayi kaman an dauko guduma an shirga mata. Cikin qasa da minti daya tayi qoqarin daidaita nutsuwarta dukka a qoqarinta na daidaita komai,ta girgiza kai tana fadin "Na qoshi". Sake ware idanunshi sosai yayi a kanta yana dubanta,abinda ya sake sanyata kenan a tsilla tsilla,tana kyautata zaton akwai wani abu me nauyi da idanunsa ke dauke dashi,wanda muddin ya kama zuzzurfan kallo irin wannan sai kajishi har qashinka. "I think kin fito ne ke debi abincin right?" Daburcewa tayi yanda ya kama abinda ya fito da ita din kansa tsaye kamar me gani har hanji. Bata saba qarya ba koda wanne irin hukunci aka tanadar mata,wannan ya sanya kai tsaye ta bashi amsa da eh. "Good.....kinga wannan shi yafi kamata muci tare ko?" Ya fada cikin sigar saukar dakai yana turo abincin gabanta. Kanta ta sake kadawa,gaba daya yana birkitata ganin yadda yake matsantawa saita zauna sunci abincin "Seat down!" Ya fada da wani irin husky voice yana buga hannunsa saman table din har abincin dake cikin plate din yana watsewa saman table din. Batasan sanda ta zauna ba kaman yadda ya buqata tana qoqarin kaucewa kallon fuskarsa da har hancinsa ya fara yin ja alamun tsananin bacin rai wajen farin mutum kenan. "Kinsan abinda zan gaya miki guda daya?" Yayi maganar qasa qasa kamar ba shine yanzu ya buga wannan tsawar ba,bai jira ta amsa ba ya dora da fadin "Duk sanda kika qara yimin girki a gidan nan saikin cinyeshi tsaf!". Gigicewa ta sakeyi da abinda yace,maganar daya fada kawai ta sanya hasashenta ya tsaya daidai inda take zatonsa "Be warned!" Ya furta yana ranqwafowa sosai saman kanta har tana iya sheqar dumin numfashinsa da yake futarwa daga hancinsa. Baya yaja ga kwashe wayoyinsa,zuciyarsa na masa wani irin zafi ya soma sauka daga wajen yana dosar hanyar da zata sadashi da stair dinsa. Maamah uwarsa ce,ba yadda zaiyi da ita,amma zaiyi dukkan abinda zai iya ya toshe kowacce qofa da zata samu nasarar budeta a kansa ko kuma waninsa muddin yana da iko da masaniya. Koda ya koma saman duk yadda yaso yayi keeping kanshi busy ya manta da komai sai ya kasa. Mahaifiyarsa......macen daya biya kudade aka daura mata igiyarsa..... A duniya idan akwai wasu mata da sukafi kowa kusanci dakai suna sama da wadannan ne?. Me suke nema a tare dashi?,amsar daya kasa laluba kenan. Sosai abun ya dinga masa ciwo,shi yasa ko sau daya bai taba aminta da ita ba,ko sau daya bai taba jin ya gamsu da ita ba......takowacce fuska tana da qatuwar lam'a da tabon da shi shine babbar shaida......bayan tarin shaidun da ya samu har abinda be nema bama an bashi,ta yaya zai iya kallonta a matsayin wankakkiya?,ta yaya zai iya yafe mata?. Yanason ya zame mata lesson me girma a rayuwarta,zai kuma ganar da ita kuskurenta na shiga rayuwarsa hakanan kai tsaye. Daga qarshe dai dole ya kunna karatun qur'ani daya karade ilahirin sassan nasa,yayi kwance kawai idanunsa a lumshe sautin yana shiga kunnensa,sannu a hankali kuma nutsuwa ta fara samuwa a jikinsa. Ko qwaqwaran motsi kasa yinsa tayi ballantana ta tashi daga wajen,batasan adadin lokutan data shafe zaune a wajen ba,har sai data daga idanu taga agogo yana gaya mata qarfe goma da rabi saura mintina biyar sannan ta iya miqewa. Zuwa sannan hatta da qafafunta sunyi wani irin nauyi da sanyi,saita gaza shiga kitchen din ta zarce hallway din sannan ta fada dakinta. Rasa abinda ya kamata ta tuna tayi,ganinta yayi kenan koko yaya?. Karon farko da taji wata irin nadama na saukar mata. Ya akayi ta biyewa mamah din ta yarda ta ciyar dashi gubar da batasan ranar yankewarta ba?,wacece maamah din?,me kuma take qullawa?,me take buqata ne a rayuwarta sama da rayuwar da take ciki?. Zafi sosai takeji cikin ruhinta,tunda take bata taba sha'awar ciyar da wani ko shayar d wani wani abu me illa irin wannan ba,koda sanda take shirya gyara zaman mazan da suka zabi harka da mata kuwa. *_DUNIYATA LITTAFIN KUDI NE(PAID BOOK),KAI TSAYE KI TUNTUBI WANNAN NUMBER_* 08187255862 𝐃 𝐔 𝐍 𝐈 𝐘 𝐀 𝐓 𝐀 _Zafafabiyar_ ̶B̶O̶O̶K ̶2 ⱧɄ₲Ʉ₥₳ 𝙋𝘼𝙂𝙀 42 _Daba abu hurairah RA yace,manzon Allah S A W yace "mafi falalar sallah bayan sallar farilla itace sallar dare_ *_ga falala ga kaifi,biyan buqata kaman yankan wuqa😄,Allah ya bada ikon jurewa_* ____________________________ ★Qarfe tara na safiyar alhamis ce wadda aka wayi gari da lullumi qwarai,sakamakon hadarin farko daya fara hada jikinsa tun bayan sallar asubahi. Bai bada ruwa ba amma kuma ya yiwa rana shamaki daga fitowa tayi rawar gaban hantsi kamar yadda ta saba kowacce safiya saman sararin samaniya. Yanayin sai ya haifar da yanayi me dadi da kuma sanyaya zukatan da suke cikin wani yanayi. A irin wannan lokacin ne muhammad jadda mamallakin kamfanin jadda diamondchore resources yake saukowa a hankali daga samanshi. Cikin shigar aiki,saidai kuma yau zaka dauka juma'a ce saboda shigar kaftan yayi. Dinkin zamani daya zauna masa sosai,ya kuma fidda sigar kyan nan nasa da kana kallonsa zaka tabbatar tabbas halfcast ne shi din wato ruwa biyu. Cikin parlor din ya samu tuni ameh ya kammala shirya masa komai na breakfast dinsa. Ameh din shi ya koma masa girki tun bayan wancan abun daya faru,yaja daya daga cikin kujerun wajen ya zauna ameh din ya gaidashi cikin rusunawa. Amsawa yayi da kulawa sannan ya fara serving nasa,yana yi yana dibansa da labarai,wanda kusan dukansu labaran da suka fita ne a jaridar safiyar. Ameh din yana da karance karance da yawan sauraran kafafen yada labarai,don haka a mafi yawan lokuta idan bai samu damar duba news paper ba shike bashi latest na cikinsu. A nutse ta maida littafin amdatul ahkam da take dubawa,ta kuma d'auki zaduzzaujaini ta sakashi a ciki don yin alama akan inda ta tsaya din. Saman side bed drawer tayi masa kyakkyawar ajiya tana jin wata nutsuwa tana ratsata. Sati guda kacal kenan da fara karatunsu da rumaisa'u d'iyar malam amma wani nutsuwa takeji da gamsuwa da karatun. Rumaisa'u din da tayi tsananin mamakin ganinta a matsayin malamarta da ya dauko mata domin daukan karatun addini a hannunta. Zuwanta kusan uku tana rejecting tana qin fitowa......sai ana hudun ta fito da zummar yiwa malamin ko malamar bayanin ta daina wahalar da kanta tana zuwa......ta gayawa wanda ya aikota dalibar bata da buqatar wani karatun. Ganin rumaisa'u din sai ya zagwanye komai daga zuciyarta,ta cika da mamakin zuwanta gidan,saidai daga baya rumaisa'u din ta gaya mata "Hamma muhammad tsohon dalibin malam ne" "Gwara da kika ce tsohon" Sabreen ta furta a ranta. Don tako ta ina bataga ta inda ya dace ko ya cancanta mugu maqetacin mutum kamar fu'ad din ba ya hada alaqa da malam ba. Daga haka ba wani zance daya qara shiga tsakaninsu,sai hiran duniya kawai da kuma karatun daya biyo baya. Da farko kawai dai tana sauraren rumaisa'u dinne,amma karatun kwata bayayi mata wani armashi ko burgeta. Saidai lokaci guda kuma a rana daya data arawa rumaisa'u hankalinta sai taji karatun ya fara shiga kanta,mafari kenan data fara hada hankalinta da zummar Tsintar abinda ta Tsinta,saidai tafi tafi sai ta fahimci karatun yafi qarfin ka tsinta kawai. Ita kanta rumaisa'u mamaki takeyi ainun....mamakin yadda karatun yake gudu saboda yadda suke qara karatun da yawa. Ta sallama da gaske karatun yana gudu ne saboda wata irin sharp brain da Allah ya bawa sabreen din,irin kwanyar da bata taba ganin irinta ba. Don duka karatun da sukayi da yammaci,zuwa wani yammaci din sabreen din ta narkashi ya koma cikin kwanyarta. Tun asali tana da bala'in son karatu,musamman na addini din,saidai wani dalilin me zuwa ya ture wani. Ratayuwar hidimar qannenta saman wuya da kafadunta ya sanya tilas ta haqura da komai ta tattara ta ajiye,a yanzun kuma data fara shiga cikin abun sosai sai takejin komai kamar an yaye mata wani hijabi ne da da ya lullube kwanya da idanunta. Tun sanda ta fahimci ya ajiye cook dinsa cikin gidan saita saita lokacin ta,sanda zata fito tayi sabgarta daga shi har cook din nasa basa gidan,hakazalika kafin su dawo ta kammala komai ta koma daki abinta. Tayi mamakin yau da taji yunwa da safe da wuri haka,to amma kuma idan ta tuna ba wani abun arziqi take ci ba musamman jiya da dare bata saka wani abu me muhimmanci a bakinta ba sai taga ba abun mamaki bane. Indonesian hijab down squeeze ta saka saman soft and cotton nigh gown din jikinta da bata fidda siffarta ba,saidai tadan lafe mata a mazaunai saboda taushinta. Hijab din ya qara qawata mata fuska,fuskar data fita sosai ta tsakiyar hijab din da wani irin kyau kai kace itama haifaffiyar Indonesia dince. Ta qarasa gaban mirror ta qara turare a jikinta dan kadan kamar yadda ya zame mata wajibi,sai ta tsaya tana duban fuskartata. Wani irin glowing skin dinta yakeyi wanda ita kanta ta rasa dalili,saidai a yawancin lokuta tana bawa kanta amsa da wataqila zaman guri daya ne,sabanin baya da kullum muddin gari zai waye rana ta fito to zata saka qafarta a waje ta fita. A hankali take tako hallway din,yau kawai tana jin nishadi cikin ranta sosai da cikakkiyar nutsuwar da batasan dalilinta ba,kwanyarta tana bitar wasu daga cikin karatuttukan data haddace,a haka ta rasa parlour na farko ta wuce zuwa na biyu. Tana murza glass door din ta sanyo qafafunta ya daga idanunsa a hankali daga inda yake zaune ya zubesu fes saman fuskarta,idonta ya shiga nasa,sai ta janye nata idon a hankali,ta kuma ja da baya tana komawa da bayan a maimakon fitowa da tayi niyyar yi. Sam bata qaunar gamuwa dashi,a kwanakin data janye kanta daga komai da zai sanya su hadu ta kama karatunta sai take samun wata irin nutsuwa a zuciyarta. Ta dauki kwanaki rabon daya sanyata cikin idanunsa,daga shi har maamah sai takeji kamar Allah ne yayi mata maganin matsalarsu. Janye nasa idanun yayi shima bayan ta koma da baya tana kuma komawa ciki. Yadan jijjiga kai kadan yana daukan mug din gabansa ya sanya a bakinsa. Tana gyara bedroom dinsa kamar yadda sukayi sharadi,saidai daga wannan ko gilmawarta bai sake gani ba tun daga ranar. Can qasan zuciyarsa tana cike da wasi wasi da kuma qiyasi akan abubuwa da dama. Sai yake zargin shurunta dana maamah dukka kamar akwai wani magana a qasa,don haka ya jawo wayarsa ya kira me sunan malam. Cikin qasa da second ashirin suka gama magana,ya shaida masa ya nema farouq ya turo amintacce kuma sirrintaccen me musu installing CCTV. Mules din qafarsa ya maida,sannan ya ciri napkin guda daya yana goge dan abinda ya bata masa hannu kafin yace da ameh. "At night.....ka dafa paw paw leaves ka ajiyemin da duminsa.....daga yau inaso ya zama first drink dina for morning". Kai ameh ya jinjina cikin girmamawa "As you wish sir". Sai ya sauka a nutse amma hankalinsa yana dan kan qofar kadan,yanason sake tabbatarwa komawa tayi ta fasa shigowa saboda yana wajen?. Murmushi ameh yayi yana binsa da kallo,sosai boss dinsa yake burgeshi,yayi aiki kafin wajensa gidajen manyan attajirai da dama,amma baiga mutum me kiyaye lafiyarsa da yasan sirrin abinci ba irin boss din nasa ba. Yasan duk wani abu da zai gyara lafiyarsa a matsayinsa na namiji,yasan duk wani abu da zai gyara masa lafiyar ido da fatarsa,hakanan yasan duk wani abu da yake natural anti aging remedies kala kala. Ire iren abubuwan da shi yake tanadarwa manyan da yayi aiki a qarqashinsu don inganta lafiyarsu da gina garkuwar jikinsu suke qin ci ko sha don ba dadi a baki ko basusan muhimmancinsa ba......sai gashi shi kullum ne sai an tanadar masa da wannan abun morning and evening. Akwai hadin salad daya dinga mamaki sanda yaga yana cinsa farkon xuwansa,musamman da yake yasan yadda yake inganta qarfi da lafiyar d'a namiji,da yawan wasu abubuwan ma shike qaruwa dashi a wajensa. Baya son maggi da yawa a abinci,kaman yadda sanyi zaqi da kuma maiqo da abokansa bane sam sam (Mata da yawa suna complain din rashin lasting din mazansu a other room,sunsha magani sunsha maganin amma a banza,anata samun sabani da sauran masu matsaloli,to wallahi wallahi da yawansu maggi shine yake kashesu,inda kinsan yadda maggi yake kashe lafiyar mazajenmu da kinyi mugun gudunsa kuwa,kiga mace ta saka farin magi a abinci,tazo ta saka wadancan cubes din kala daban daban,ta hada drink ta laftawa miji sugar,ga uban sanyi,abinci mai yana kwanciya,ba ruwanki da manja ma sam sam,to billahillazi kunji na rantse muku haka zaita zame miki mace,kuma duk irin maganin da zaisha fa a banza,muddin ana kan cin magin nan,tashi daya ba zaki iya dainawa ba,amna gradually zaki dinga janyewa,idan goma kike sawa ki koma bakwai daga haka ki koma hudu,tabbas indai zaki dimanci haka zaki ga canji,ki ajiye farin maggi kwata kwata,zaqi da maiqo duka ki rage masa,hadin wancan salad din in sha Allah zan kawo muku shi a gaba,ya gwada cin na sati biyu bayan kin janye magin kiga ikon Allah,koda me gida yana da lafiya ma normal ne kina iya hada masa shi ya dinga ci,amma ina maimaita muku ku raba kanku da kayan d'an d'anon nan,Allah yasa mu dace). Kamar kowacce safiya muddin yana da isashen lokaci......ba baqi ba meeting na early morning da sauransu,zuwa duba lafiyar anni da gaida maamah din yana cikin schedule dinsa na kullum. A farfajiyar gidan kamar ko yaushe ya samu guard dinsa,kowa na tsaye akan aikinsa. Bai qaraso bama amma tuni Jordan ya buda masa bugatti dinsa yana jiran qarasowarsa. Cikin girmamawa da nuna kulawa suka gaidashi ya amsa yana bincikar lafiyar kowa kaman kowacce safiya,sai daya tabbatar da kowa lafiya sannan ya miqawa saddiq da kusan a makare yake isowa kayan hannunsa,wannan dalilin ya sanya baya samun shiga cikin gidan duk zuwan da yakeyi. Sun dauki hanya sosai kiran musaddiq ya shigo masa,ya fidda wayar yana connecting nata da Bluetooth dinsa yana amsa wayar. "Hamma na gama komai......sai yaushe zan dawo?" Musaddiq din ya amsa a karye da alama gida yakeson dawowar. "Ka dawo kayi me?" Ya tambayeshi yana jin tantama a dawowar tasa. "Hamma nayi missing anni......nayi missing saddiq". Iska kadan ya furzar daga bakinsa wadda ta fita da qamshin mint leaves saboda mouth fresh dinsa kenan na dindindin " Anni kuna waya haka saddiq.....kuma ko ita nasan bata da damuwa me yawa a tafiyarka.... Dude ne kawai nakeji ban kyauta masa ba dana dauke masa personal assistant......shima nasan ya fahimceni.....oops......anyways......nan da sati biyu zamu hade a madeena in sha Allah,it was family trip time". Har a muryarsa yaji dadi "Hamma na Manta da lissafinma.....okay..." "Hope komai naka ba matsala ko?,daga can zaka iya shiga koda Jeddah ne sai ka qaraso madeena" "Direct entry zanyi hamma.....i can't wait to see my family". "Alright....ka kula da kanka" Ya furta cikin kulawa "Na gode hamma" Ya ambata suna ajiye wayar. Wayar ya zubawa idanu yana tuna wasu abubuwa da suka shude..... Ita rayuwa dukanta tana komawa tarihi ne watarana......bai taba zaton a rintsin da suka fuskanta shi da musaddiq ba akwai ranar da zatazo kamar haka komai ya wuce ba......yadda kula da musaddiq da bashi rayuwa me kyau ya sanya hannuwansa sukayi kanta.....tunaninsa ya dimauta,kwanyarsa ta kusa jirkicewa da daina iya tuna kome me kyau.....ambaton sunan maamah ya zame musu kamar wata jarabawa. Hannunsa yasa ya shafi fuskarsa yana son ajiye tunanin a gefe.....yanzu yanzu zai iya rasa kowacce nutsuwa tasa,ya kuma rasa duk wani courage na aiki daya fito dashi a yau din. "Gidan maamah zai fara tsayawa" Yace da saddiq don ya shaidawa driver din shi kuma ya sanar da ayarin motocin. Yayi hakanne don yasan muddin ya shiga gidan maamah a yanayin da yake ciki na tuna munanan abubuwan data aikata baga rayuwarsu kadai ba......anni itace zata zamewa zuciyarsa yayyafin ruwan sanyin da zai wanke duk wani baci da ransa yayi. Kamar kullum da qafa ya taka daga inda suka ajiye motocin zuwa cikin gidan. Malam sa'adu ya matso da sauri yana bude masa qaramar qofar kasancewarsa shugaban masu gadi na gidan a yanzu. Tunda aka mallakawa maamah din wannan gidan yafi qarfin gadin malam sa'adu shi kadai,dole sai daya hada mata da security,amma kuma kowa yana qarqashin malam sa'adun ne wanda shike da permanent chair. Har kullum burgeshi hali da dabi'ar muhammadun takeyi,ya taka dukkan wani matsayi da bawa zaizo ubangiji ya kaishi a rayuwa,amma bai dauki hakan a bakin komai ba. Gaisawa sukayi kamar kullum,sannan ya taka yana shigewa cikin gidan da ma'aikatan dake bakin aiki kowa yake zubewa yana gaidashi. Daidai sanda yake sallama a falon daidai sanda take fitowa daga kitchen din gidan,Hannunta dauke da qatuwat warmer kamar ma rinjayarta takeyi. Huda ce,ta bishi da kallo tana amsa sallamar tasa cikin kallon baqunta. Yadan sake dubanta kadan,sai yake jin kamar yasan fuskar,amma kuma sai ya kauda wannan tunanin yana neman wajen zama,daidai sanda take gaidashi cikin ladabi daya zame musu jiki tun tale tale "Ina kwana?" Ko daya maida dubansa kanta sai yaga har ranqwafawa tayi irin na ban girman nan "Lafiya la....." Amsa gaisuwar ta katse saboda yadd warmer din taso subuce mata daga hannunta. Cikin zafin nama ya isa ya karba yana fadin "Kibi a hankali......" Sai ya taka yana kaita saman dining din ya ajiye. "Maamah ko?" Ta tambayeshi qasa qasa kaman me tsoron tambayar,don itadai yana mata kama da mijin adda sabreen din su. Kai ya jinjina kadan a ransa yana mamakin ina kuma maamah ta samota?. "Bari na kira maka ita" Ta fada da dan saurinta,can qasan ranta yana cike da murna,yau kam taga wani daya danganci addansu.....ko gaisuwa ta aike mata tunda yawan lokuta maamah tana cewa ta kira basa kusa. Wayar hannunta da maamah ta bata kuwa da komai akai,hasalima suna waya kusan kullum da momma bahijja,amma batasan me yasa number adda sabreen din kota kira sam sam bata shiga ba. *_DUNIYATA LITTAFIN KUDI NE(PAID BOOK),KAI TSAYE KI TUNTUBI WANNAN NUMBER_* 08187255862 43 _Daga anas dan malik R.A yace:an rawaito daga manzon Allah S A W,ya 'yanta matarsa SAFIYYA,kuma ya sanya 'yantata din a matsayin shine sadakinta_ _bukhari da muslmin suka rawaito_ A step na biyu taga maamah din tana saukowa daga saman,hannunta cikin na haneefa daketa bata labari. "Yammatana ya akayi?" Ta tambayi huda tana dan sake mata murmushin nan nata da kusan sun sana dashi. "Baqo ne kikayi" Ta fada tana dan waiwayawa inda fu'ad ke zaune,hannunsa dauke da remote yana sauya tasha,bawai kuma don yanason kallon bane aah....sai don kawai bayason kallon fuskar maamah din sakamakon abubuwan daya tuna da suka motsa ranshi. "Muje to" Ta amsata har qasan ranta tana jin dadin yadda huda din ta kasa gane wanene. Tanason sanyata ta koma daki don kada suyi wata magana da zata fahimci wayeshi a wajensu?,amma kuma ta rasa wanne uzurin zata bata tunda dai abinci zataci akan dining. Uwa uba kowanne motsi nata da maganganunta tana yinsu ne a ankare,bata bari tayi wani abu da zai sanya shakka a ransu ko ta gaza juyasu yadda takeso. Tunda suka sauko din haneefa ta zubawa fu'ad ido. Tabbas shine mijin adda sabreen,ta ganshi har sau biyu bata kuma mance ba,sannan bata sake ganinsa ba sai yau. Saman kujerar maamah ta zauna,haneefa ta zauna a gefanta still idanunta suna kanshi ta kasa daukewa. Sanda ya gama gaida maamah din sai nasa idanun suka sauka akan yarinyar. Kamanninta suka fusgi idanunshi sosai,ya sake ganin wata kamar ta daban bayan wadda ya baro dazu tana me komawa falo bayan sun hada idanu. Murmushi haneefa ta sakar masa sanda taga shima ya dan kafeta da ido. Ya murmusa kadan tana shirin janye idanunsa sai yaga ta zame tana fadin "Ina kwana mijin adda sabreen?". Kallon mamaki yake bibta dashi,mamakin da bai gama sakinsa ba tace "Sunana haneefa nice autan adda sabreen,'yar mitsisiyar dakinmu". Baisan ya akayi murmushi ya ratsa miskilar fuskar nan tasa ya bayyana ba,ashe masu son sarautar autancin suna da yawa. Yanayinta sak sai ya tuna masa da yanayin amna. " Ya isa haka haneefa....kije kuyi break ko ki koma daki wajen nadra ku kalli cartoon" Maamah tayi hanzarin dakatar da tattaunawar tasu. A nutse ya cira kansa yana duban fuskar maamah din,haka kawai sai yaji yana da buqatar ci gaba da magana da yarinyar. "Qyaleta muyi hira maamah....she's very smart" Ya fada da wani irin tone a muryarsa,wasu abubuwa da wani irin gudu suka fara bijiro masa,yayin da gumi ya fara tsargawa maamah ta cikin rigarta. Ta sani,tafi kowa ma samin haneefa she's very smart,fiye ma da zatonta,wannan ya sanya tafi janta a jiki da kuma kaffa kaffa da ita. "Indai surutun haneefa ne saika gaji dashi......ni kuma magana nakeso nayi dakai,next time idan kazo sai kuyi hirar" Ta fada tana dan hade rai gami da gyara zama. Sake dubanta yayi a karo na biyu,abubuwa biyu suka hade masa waje guda. Har yanzu dabi'ar nan tata tarashin son yara tana nan?,banbanci qarara me kuma fadin gaske na farko tsakaninta da anni. Indai haka ne yara uku ne cikin gidanma kenan?,akwai daya a cikin daki?. Me ya kaita dauko yara har uku?,ita da basu dameta ba?. Meye abun damuwa don yana hira da yarinya qarama?. Agogonsa ya kalla,sai ya maida dubansa ga fuskarta. "Ba damuwa ai,yau muna da enough time sama da kullum". Kafin ya sake cewa wani abu haneefa tace " Zaka kaini naga adda sabreen?......don Allah hamma kada kace aah" Ta fada tana narke murya. Maganar taja hankalin huda dake saman dining,itama saita ajiye spoon din abincin da takeci ta maido hankalinta kansu. Gumin dake tsatsatsafowa maamah din ya sake yawaita,da sauri kamar ana tankadata tace "Aah fa haneefa......ni da kaina mukayi zan kaiku haka ne?". "Eh amma har yanzu baki kaimu ba maamah,shi kuma hamma ma daga can yake ko?" Ta maida tambayar kansa. Kansa ya gyada a nutse yana karantarta. "Maamah ki barshi ya kaimu ko anjima ne,in yaso saimu dawo da kanmu" Huda itama ta saka baki,don da gaske sunyi tsananin kewar sabreen din. Sanda ta waiwaya da nufin yiwa huda din magana sai maganar fu'ad ta dakatar da komai. "Jeki dauki hularki kuzo muje nasa a ajiyeku" Yayi maganar kansa tsaye,maganar data daki tsakiyar kan maamah da wani irin ba zata. Har ga Allah kanshi tsaye ya fada kuma hankalinsa kwance,kawai dai a cikin zuciyarsa ya dade da rashin aminta da kowanne motsi na maamah din. Bashi da gamsuwa akan abubuwa da yawa sa suka shafeta,shi yasa a kusan komai idanu da zuciyarsa suna akai. Cikin qasa da minti uku sai gasu kowacce da mayafinta. Dab da zasu fita daga falon ta kirayi sunan huda da yanayin da tunda hudan tazo gidan bata taba gani cikin muryarta ko sautinta ba. Fuskarta a dinke ba fara'ar nan da suke kwana suke tashi da ganinta akan fuskarsu "Kada ku wuce ko ina,daga can ko dawo gida,zanwa driver magana zai biyo bayanku,karku wuce awa daya......." Idanu huda tadan zuba mata,sai kuma kawai ta gyada kai mamakin sauyawar maman tana kamata. Tasha musu alqawarin fa zata kaisu.......sai kuma daga baya tace ai wani uzuri ne ya taso sai bayan wani lokaci,duk da ta lura akwai permanent driver a gidan da yake zaune baya aikin komai. Yana zaune daga cikin motar saidai qafafunsa suna a waje ba'akai ga rufe masa murfin ba suka fito. Yadan daga kai ya kallesu,dukkaninsu suna kama da ita saidai qaramar ta fisu daukan kamanni sosai da ita. Mamaki kadan yana dan kamashi na ganin banbanci muraran tsakaninsu. Dukkansu da alama suna da sauqin hali da kuma tarbiyya sosai,don ba wanda ya gaidashi a tsaye a cikinsu saida suka rusuna "Ta fita zakka kenan" Ya gayawa kansa da kansa yana sauko qafafunsa qasa ya fito waje. "Abdulgaffar" Ya kirayi shugaban tawagar tsaron nasa,ya matso da gaggawa yana rusunawa "A cire mota daya a sakasu a kaisu gida" Ya bada umarni hankalinsa yana kan kiran fareeda dake shigo masa. Kaman yadda baya gajiya da qin dagawa hakanan itama bata gajiya da kiran nasa,yaja wani dogon tsaki yana komawa motar,ranshi yana tsananin baci da kalar wannan kiran nata da dukkanin numbers dinsa,kamar wadda batasan abinda ya dace ba,baisan ma ya akayi take da dukka numbers din nasa ba. "Soulmate" Sunan da tayi kiransa dashi kenan da wani irin salo na kashe murya da jan ra'ayi. "Why?.....ke bakya gajiya da kira ne?,it's so annoying.....please don't do it again.....stop it" Ya fada da sautin bacin rai a muryarsa. "Haba ka fahimceni mana" Ta sake fada da hanzari cikin tsoron kada ya katse mata wayar..... Kada ya ajiye wayar bayan ta samu dama ya daga wayar bayan dukka wahalar da tasha "Na fahimci me?....ke bakya ganewa cewa macace ke?,ke ya kamata abi bawai kibi ba?.....kina mantawa mace da kamun kai aka Santa?.....". Da sauri take girgiza kai "Indai a kanka ne bani da wadannan qualities din....." "Okay....then karki sake kirana....." Yaja qaramin tsaki yana yanke kiran hadi da jan dogon tsaki yana wurga wayar gefe. Gaba daya soyayya tana sake tona masa kanta a matsayin wani abu da yafi komai zama matsala da takura a rayuwa,shi yasa bazai bari ta kunno rayuwarshi yanzu ba har sai sanda ya shirya ya kuma kebe mata lokaci nayin nata. Idanunshi akan motar BMW din da aka sanyasu a ciki,sai da yaga fitarsu a gidan sannan yayi musu umarni suka tashi motocin suna fita suma daga layin. Sauke labulen window din da yake bata daman ganin farfajiyar gidan tayi cikin wata irin matsananciyar fargaba da kuma tashin hankali. Gaba daya kowacce idea tata ta kunce,ta rasa wanne zaren tunani zata kamo?. Wacce irin baqar rana ce yau?,wanne tsautsayi ne qaddara ya sanyata lokacin shigowarsa ya kubce mata har ta saki yaran haka?. Idanunta ta mayar saman agogo......sai a sannan ta lura,yau ya sabawa lokacin shigowar tasa ne,ya shigo da wuri ba kaman yadda ya saba ba,sai tasa hannu tana sharbe gumin fuskarta da tafin hannunta. Da dan hanzari ta taka da kanta tana fita farfajiyar gidan tana qwalawa mansir kira,kiran daya sanyashi sakin duk abinda yakeyi ya qaraso babu shiri. "Ka fito da mota,kabi bayan motar jadda diamond zuwa gidan muhammadu......akwai yara da sukaje gaida matar gidan,suna shiga minti goma kacal ka aika su taso ka dawomin dasu......mansir?,idan ka kuskura aka samu akasi baka maidominsu akan kari ba to ka kuka da kanka......ban yarda ku biya ko ina ba......ban kuma yarda ka ajesu ako ina ba" Ta fada tana zare idanu tanaji a jikinta tamkar wani abu zai faru. "In sha Allahu ba zaa samu ko daya daga ciki ba" Daga haka saita juya tana komawa ciki. Kasa zama tayi ko a cikinma,a jikinta takejin kamar akwai wani abu da ba daidai ba "Ki kira zuwaira kisa ta kula miki da motsinsu" Wani sashe na zuciyarta ya bata shawara. Bibbiyu ta dinga hada stairs din tana haurawa samanta,cikin lokaci qanqani ta isa dakinta,ta zauna gefan gado tana daukan wayarta dake saman drawer ta fara kiran zuwairan. Saidai kash!,kiran farko aka shaida mata kwata kwata wayar a kashe take,ta sake gwadawa cikin rashin gamsuwa da bayanin farko na na'urar......still sukace mata yana a kashe,ta sake dai gwadawa a karo na uku,nan dinma amsar dukka daya ce,saita ajiye wayar a gefanta tana jan wani matsiyacin tsaki 44 _Daga hassan dan sumra R A yace,daga manzan Allah S A W yace:Duk macen da waliyyai biyu suka aurar da ita ga maza mabanbanta a lokaci guda,to ita din mallakin na farkon ce(wanda aka fara daura mata aure dashi)_ "Tur da halinki zuwaira,Allah wadai da halinki" Ta fada tana cika tana batsewa,har cikin ranta tana jin kamar tayi tsuntsuwa ta tafi gidan da kanta. To amma kuma idan tayi duba ga wasu abubuwa,hakan bame yiwuwa bane,dole taci gaba da zama tana gwada kiran akai akai,yayi da idanunta ya ta'allaqa akan agogo tana qidanye da mintunan fitarsu daga gidan. Daga qarshe ta sare kan samun xuwaira,to amma dole tana da buqatar kiran wani da zame zame mata garkuwa a can gidan "Laila" Zuciyarta ta tunasar da ita. "Yauwa" Ta fada da madaukakin zumudi,ta soma lalubar number wayar lailan. Duk da safiya ce amma ta kusan awa guda da rabi a gidan nasu. Cikin asalin dakin da yake shine mallakinta,saman gadon sun qule ita da mahaifiyarta hajja harira wadda ta tsareta da idanu bayan ta gama zayyane mata karonsu da fu'ad na qarshe. Sai da tayi kaman ba zata daina kallon nata ba kafin taja wani tsaki tana dauke dubanta daga kanta. "To wai meye ma amfanin zamanki a gidan laila?,kada ki zama albasa mana wadda batayi halin ruwa ba?,na kaiki gidan badon kin rasa wajen zama ci sha ko sutura ko kuma gata cikin naku gidan ba.....na kaiki ne saboda ki karanci komai.....ki haddace komai ki kuma bi kowanne taku da motsi na kowa a gidan kafin mu fara gabatar da namu shirin koda kuwa.mariya batayi nasara ba......nasarar mariya ko faduwarta ba damuwata bane.....hasalima inda zata fadi hakan shine daidai a tare dani......kinsan me?" Kai laila ta girgiza tana jin faduwar gaba da kiran sunan maamah da akayi. "Nasarata itace ya kamata ta fara samuwa......nasarata ita ya kamata ta fara wanzuwa kafin ta mariya........ni ya kamata na fara samun fu'ad na mallaka miki shi......muddin mariya ta rigamu samun fu'ad to ba shakka dukkan wata nasara da muka sanya rai a kanta zata iya zuwa mana da tsauraran hanyoyi da matakai......shan kai nake da buqata mu yiwa mariya laila.....donme kikaje kika kwanta kina bacci?,waye ya gaya miki nasara na zuwa ta sameka har inda kaka?,bakisan fita ake a nemota ba?!" Tayi maganar da alamun qunan rai a cikin muryarta,hatta kuma da lailan ta karanci haka,saidai batasan me yasa a kwanakin nan takejin sam bata da damuwa akan wannan lissafin na hajja ba......tamkar wannan lissafin an zare mata shi kwata kwata daga zuciyarta. "Ban sauka ba hajja......kawai dai saina dinga jin kamar idan mukayi hakan bamu kyautawa maamah ba,kamar idan mukabi komai a sannu zaifi....." . Baki kawai hajja harira ta sake tana kallon laila da wani mamaki daya taru a fuskarta,kuma koda ta zubawa lailan idanu saita karanci da gaske take maganar. Tana shirin yin magana aka turo qofar aka shigo. Madeena ce dauke da serving tray data jero dukka kayan dadin da aka dafawa hajjan a matsayin abincin safe. Tun asuba take tsaye don kawai ta faranta mata,kuma bata da tabbacin zata yaba ko kuma tayi accepting abincin gaba daya. "Gasu hajja an gama....." Ta fada tana rusunawa ba tare data iya hada ido da ita ba. Wani abu me nauyi da girma ya riga ya sauka a zuciyarta game da zancan laila,don haka bacin ran daya taso mata maimakon ta huceshi akan laila sai ta fara ragewa akan madeena "Wannan wanne irin iskancin banza ne?,ina ciki muna sirri da yarinya saiki wani bankowa mutane daki?". Murya a karye cike da ladabi tace "Kiyi haquri,kin manta ke kikace idan na gama na kawo miki a daki zakici" "Naji da Allah.....koma dashi ki aje saman table......tsnnnnn" Ta qarasa da tsaki. "Awnnn..... Me dame kika dafa mata ne?" Laila tayi tambayar tana maida dubanta ga madeena wadda je tiri tirin fita da tray din. Ido kawai hajja ta zubawa laila tana mamakin yadda take nuna halin ko in kula da magana me muhimmanci irin wannan. Dawowa madeena tayi ta durqusa ta bude mata dukka bowls da warmers din,sai lailan ta karyar da wuya. "Wallahi meat pie nake mugun kwadayin ci da safen nan.......don Allah hadamin yaji naman rago cikin sosai" Ta fada kanta tsaye da sigar umarni. "Tom" Madeena ta amsawa lailan wadda a qalla tayi qanwa ta hudu da ita,ta miqe ta kwanukan tana sauka. "Idan da a rayuwa tsaiwa ake duba abinda ya kamata......inda a rayuwa jira ake sannan ayi abinda ya dace........tabbas ke kanki da baki juya matan yayunki kamar haka ba" Hajja tayi zancan tana tsare laila da ido tare da qoqarin maida mata girman zancan cikin zuciyarta. Dan muskutawa laila tayi tadan kashingida,har yanzu a ranta ita batajin damuwar komai,duk da kuwa bayan kowacce daqiqa sai hoton kyakkyawar fuskar nan tasa ta gilma ta gaban idonta,abinda ke sakata sakin ajiyar zuciya lokaci lokaci gami da sakin qaramin murmushi. "Inaso komai sauya.....inason ki canza akalarki daga yau.......dole gobe ki dawo ki karbi naki kayan aikin......ki kula da zuwaira......banason tasan komai.....bana son kuma ta fuskanci komai" Ta fada tana tsareta da ido. Saidai bata kai ga amsawa ba wayarta dake saman kanta ta dauki tsuwwa. Tana daga kwancen ta daga kanta tana duban me kiran,saidai ganin sunanta kadai ya sanyata wani irin zabura hadi da tashi zaune. Hakan kuma baiyi mata ba sai data zamo daga saman gadon ta durqusa a qasa sanda take daga kiran hade da sallama. Dukka wadannan abubuwan da tayi su suka ja hankalin hajjan sosai taji tanaso taji da wanne mutum me matuqar girma da daraja haka a rayuwarta take waya?. "Ina kwana maamah.....kin tashi lafiya?,kiyi haquri inata zuci zucin na kiraki na gaidaki da safen nan.....amma na kasa tuna waye zan kira". Maganar ta yiwa maamah banbarakwai,to amma bata wani kawo komai a ranta ba,duk da laila bata taba mata magana da ladabi rusunawa da kuma kirki irin haka ba "Ba komai,kina gida ne zan baki wani aiki?". Rawa jikinta ya hauyi saita miqe tana daukan mayafinta "Bana gida maamah.....amma bani minti goma sha biyar yanzu zan isa gidan,saiki gayamin abinda kikeso ayi miki ko mene". Mamaki kadan ya sake kamata,to amma a yanzu garkuwa kawai take nema don haka ta amsa mata da "Okay......idan kika isa ki kirani" "Ko kibar wayarma kawai on hold karki kashe yanzu yanzu zan isa,zanyi sauri ma saboda agama komai da wuri". Wani mamakin dai still ya kamata,amma sai tace " Zan sake kiranki" "To" Ta amsa mata tana sauke wayar. Jakarta ta kaiwa sura,kamar ma ta manta da hajja dake wajen,kowanne sashe na jikinta rawa yakeyi,ta jefa wayar a jaka ta rataya tana yafa mayafinta. Sai a sannan hajja da mamaki ya kasheta ta kira sunanta da qarfi "Waike da waye kike waya haka lokaci guda hankalinki ya tashi?". Murmushi ta sakarwa hajjan sanda take saka takalminta "Maamah ce fa?,ta tambayeni ne ina gida?,wani aiki zata sakani kinga ya kamata na koma ai.....bai kamata ma ace na fita ban tambayeta ba,amma zan bata haquri daga baya.....hajja na tafi,idan na gama mata da wuri zan tambayeta,idan ta barni gobe na dawo zan dawo". Mamaki da ganin almarar abun ya hanata cewa komai,ta sanqame a wajen kawai baki bude tana bin laila da kallo wadda keta sambada sauri kamar zataci da baka. *_turqashi?,wai meke faruwa?,nace meke faruwa ne jama'a?,shin qaiqayi ne koma kan masheqiya ko kuwa yaya?,wanda lamarin nan ya yiwa dadi ya danna 1😂,wanda baiji dadi ba ya danna 2_* *_gasu huda a hanyar zuwa gidan addansu,yaya zata kasance kenan?_* *_yanzu wasan zai fara tafiya daidai💪🏽_* *_muje zuwa🙌🏽_* 45 _Daga nana Aisha R.A tace:manzon Allah S A W yace:Duk matar da tayi aure ba tare da izinin waliyyinta ba,to aurenta batacce ne,idan mijin ya tare da ita taci sadakinta saboda halastar farjinta a gareshi_ Ware idanunta tayi sanda ta isa dining area,sai ta tsaya cak tana sake ware idanunta da kyau tamkar wadda bata gani sosai,kwanyarta na gayawa zuciyarta kawai yaudarar kanta takeyi,basu huda dinta bane.....ba nadra a wajen......auta haneefa tana hannun waccar azzalumar "Adda.." Muryoyinsu suka zame mata kamar tsani a gareta na tashi daga wani dogon mafarki,kamar wadda aka daki bayanta,sai ta fara nufarsu tanason ta tabasu don ta tabbatar shin su dinne?. Allah ne kadai ya sauko da ita daga steps din,don qafafunta hardewa kawai sukeyi har zuwa sanda ta isa garesu. Haneefa da tafi kusa da ita ta jawo,ta miqa hannu tana shafar fuskarta,sai kuma taja hannun huda ta riqe d kyau,sannan ta dafa kafadar nadra. Murmushi suka fara yi mata,da alama sun gane abinda take nufi,kuma dariya sukeso suyi mata,saidai yanzun ba Lokacin dariya bane. "Ku tsaya a nan ina zuwa" Shine abinda ta fada kenan tana juyawa ciki cikin gudu gudu sauri sauri. Ko ina a jikinta rawa yakeyi,batasan ya akayi suka kubuto ba,tana ji a jikinta addu'ar data tsananta a wannan Lokacin Allah ya karba mata. Birkice closet dinta tayi wajen neman hijab daya tamkar idanunta basa gani,da qyar idanunta suka nuna mata wani ruwan sararin samaniya,ta sanya hannu ta fuzgoshi ta saka,sannan ta dawo falon. "Ku taso......ku taso mj tafi" Ta fada da wani irin hanzarin daya sanyasu tsaiwa kawai suka zuba mata idanu,har sai data fusgi hannun nadra da haneefa sannan huda ta biyo bayanta a mamakance. Tana riqe da hannuwansun take ratsa farfajiyar gidan,girmanta yasa take ganin kamar ba zasu fita daga ciki ba maamah zata riskesu,kamar tayi nisa da yawa. Security da sauran ma'aikata nata zubewa suna gaidata,amma ita ba wannan bane a gabanta,don ko gane gaisuwar nata basa yi. Kai tsaye kuma a karon farko security suka bude mata gate ta fice. Taci gaba da jan hannunsu da wani irin sauri da kaf rayuwarta bata tana yin tafiya da irinsa ba "Ina zamuje adda?,ko zama baki barmu munyi ba?" Haneefa ta tambaya adan shagwabe saboda saurin da suke zubawa din ya fara isarta "Zaki gani auta......karki damu" Ta ambata tana duban hanya,daidai sanda ta hangi tahowar motar da tafi mata kama da motar da akan kawo maamah a ciki. Hagu da damanta ta duba,ba wani gurin labewa. Unguwa ce da dukka gine ginenta ke bisa tsari,layukansu shimfide da wadatacciyar kwalta,manyan gidaje da kowanne gate yake a kulle dame gadi ko kuma kare. Cikin ikon Allah ta hangi gida daya da qaramar qofar dame gadi kan fito a bude,saita jasu zuwa can ta kuma turasu ciki itama tana me shigewa. A gabanta motar tazo ta wuce da gudu,saita sake kamo hannun haneefa tana cewa "Kuzo mu tafi" Zuciyarta na tsananta bugu qwarai. Sai da sukayi tafiya me nisa kafin su samu adaidaita sahu,kasancewar unguwar unguwace ta masu kwalli masu hannu da shuni,zai wahala kaga abun hawa na haya a cikinta. Koda zai shigo ma sai ainihin security da suke gadin unguwar sunyi checking sun tabbatar da amincinsa da ingancinsa. Basa wasa ta wannan fannin saboda dukka unguwar manyan mutane ne a cikinta. Sai data tabbatar me abun hawan yayi nisa da unguwar sannan ta sauke ajiyar zuciya,ta juya a hankali tana kallonsu sai taga dukkaninsu ita suka zubawa ido,da alama qarin bayani suke nema. Murmushi kawai ta saki,ta dora hannunta saman kansu ta shafa tana cewa "Zakuji komai......bari mu isa". Kamar yadda zama ya gagareta haka tsaiwar ma sai taji kamar tana neman gagararta. Wani tashin hankali takeji mara misaltuwa,yaran su kadai ne hope dinta,idan har tayi loosing yaran tabbas bata da wani sauran hope. Yadda take juya yarinyar tayi imanin bawai girman asiri bane.....don dama ya bata tabbacin abun bame qarfi bane,idanma me yawan addu'a ce kwana uku zai saketa. In kuma me qarfin kurwa ce da tsananin hasken taurari sati biyu zuwa wata daya zai iya sakinta. A yadda take maida mata magana da tsananin izza da rashin tsoro,ta tabbatar komai ya saketa,kawai tana biyeta ne saboda yaran da suke hannunta.......idan babu su ya zata kaya mata kenan?. Wani tashin hankalin ya sake rufto mata data tuna da waya fa a Hannun huda. Ita ta siya mata ita sati guda daya wuce kenan data sake jawota jikinta. Yau idan sukayi amfani da wayar suka kira wani fa?. Abinda ya sakata rarumar tata wayar don sake kiran zuwaira ta karbo mata wayar ko da qarfi ne,tana me manta ma wayar zuwaira din a kashe take. Cikin sa'a bugu biyu ta dauka,muryarta na nuna alamun bacci. Ashar ta lailayo mata wanda ya sanya zuwaira miqe ta zauna da duwawunta "Dama bacci na aikeki kiyi?Kinsan aikinki kuwa?,kinsan muhimmancin abinda na aikeki kiyi zuwaira?!" Maamah ta tambaya a tsawace tana jin kamar ta jawo zuwaira daga cikin wayar ta zabga mata mari. Rawa jikin zuwaira ya dauka,batason tayi asarar maamah tun yanzu alhalin bata samu tudun dafawa ba. "Kiyimin aikin gafara hajiya......tuba nake" "Ki rufemin baki,ki tashi ki dubamin cikin gidanku,daga parlor din matar gidan har bedroom dinta,akwai qannenta da sukazo,ki fara karbamin wayar hannun babbar,minti goma kuma nace ki qara musu su taso ki biyosu har sai kin kawominsu gidannan". "Angama ranki ya dade" Ta fada tana miqewa da hanzari har dankwalinta yana faduwa,duk da ranta a bace yake ainun da irin tsawar data daka matan. Parlor ta duba na farko dana biyu duka ba kowa. A kitchen ta samu ma'u tana juye mata kunun a flask gudun kada yayi sanyi jin shuru bata dawo ba. Ido suka hada mau ta dauke dubanta a wajen. Haka kawai jininsu baizo daya da zuwairan ba,duk da ma'u bata nuna mata komai,saidai ita zuwairan cike take da haushin ma'un ganin yadda sabreen din ke mu'amalantarta sama da yadda take sakar mata. Ko ina na gidan ta duba,tana shirin fita farfajiyar gidan ta duba can sai ga laila ta shigo afujajan "Ina matar gidan?" Lailan ta tambayi xuwaira. "Ban sani ba nima" Ta bata amsa cikin jin haushi zuciyarta tana raya mata itama aikin dubata ta bata. Dole data gama dube dubenta ta dawo parlor din,daidai sanda ma'u ta kammala komai tazo ta rabesu tana ficewa abinta ba tare da tace da kowa komai ba. Dukkansu qoqarin kiran maamah suke don kowa ya fara shaida mata yadda ake ciki. Laila ce ta fara samunta,cikin tsananin biyayyar data sanya zuwaira sakin baki tare da tunanin ko wani sabon makircin shiga jikinta suka qullo ta tsaya tana dubanta "Maamah kaman bata gidan nan fa?". Wata zazzafar zufa ce ta karyo mata,taji kamar gudawa zata tsinke mata. To amma yaushe suka shigo da har za'ace basa cikin gidan?. "Kun duba ko ina da ina?" Kai laila ta girgiza tana duban hallway din "Banda bedrooms dinta" "Me kuke jira?,ku dubamin har can" Ta bata umarni a tsawace har sai da wayar hannun lailan ta kusa faduwa. "Zan shiga na duba" Lailan ta fada tana duban zuwaira. Wani kallo ta watsa mata tana samun daya daga cikin kujerun ta zauna tana tabe baki. Da karsashinta ta soma nufar dakunan,har cikin ranta tana jin dokin shiga taga dakunan ya suke?,tunda koda hallway din bata taba takawa ba bare akai ga shiga ciki. "Alhamdulillah" Ta samu kanta da furtawa lokacin dame napep ya ajiyesu a qofar gidan. Sai a sannan hankalinta ya dawo jikinta,ta tuna bata riqo komai a hannunta ba. "Don Allah dan yi haquri,bari a karbo maka kudinka,fitar ce ba'a tsanake ba" Ta fada tana dubansa. Bai wani damu ba sam,saboda yanayinta kadai ya tabbatar masa idan bai samu qarin abinda ya kamata a bashi ba to tabbas ba za'a rageshi da komai ba. Waiwayawa tayi ta kalli su huda "Ku shiga ciki ku karbomin dubu biyar wajen titi". Huda ce tayi gaba suka bita a baya. Basu jima ba nadra ta fito da kudin ta miqawa sabreen din,ta karba ta bashi sannan suka wuce cikin gidan a tare. Tana sallama aishatu ta fara gani,tana duqe tana wankin uniform dinta daga can bakin famfon da akayi musu saboda hidima irin wannan. Tadan zubawa yarinyar idanu farinciki yana ratsata. Ko a iya aishatu kawai idan ta kalla tana jin wani farinciki da sassauci yana ratsata,kamar ba aishatun da aka debe tsammani da rayuwa da ita ba,kamar ba aishatun da idan ka fita ba zakayi tsammanin zaka dawo ka sameta a raye ba. Sai data dago don yin shanya suka hada idanu,ta watsar da uniform din,ta rugo da gudu tana kiran sunanta "Adda sabreeennn" Ta maqaleta da kyau,sai itama ta tsugunna tana rungumeta cikin jikinta qwallar farinciki na sauka a idanunta. "Aishatu......haka kika koma?......alhamdulillah" Ta fada tana shafa sumarta me santsi. "Adda na warke.......na samu sauqi adda" Ta fada itama tana kwantar da kanta a kafadarta. "Ki barta ta qaraso ciki mana aishatu" Muryar titi ta ratso kunnuwansu tana dubansu cikin murmushi,daga nesa kuma tana kallon yadda sabreen din tayi wani irin kyau,fatarta ta qara tsananin haske da wani irin murjewa,sai glowing takeyi duk da tadan fada kadan qibarta ta ragu. Tana riqe da hannun aishatun suka shiga parlor din titi. Duka sauran yaran falon suka miqe don basu fahimci ita ake magana ba. Dukkaninsu suka baibayeta suna qoqarin kiran sunanta,sai ta zame kawai ta zauna tana rungumesu cikin jikinta gaba daya tana kiran sunansu daya bayan daya. Ruwa da lemon zobo da titi din ke saidawa ta dire musu tana zama gefanta. Sai a sannan yaran duka suka tashi suna ficewa don basu sarari. "Banyi zaton sake ganinki nan kusa ba" Titi ta fada bayan sun gama gaisawa da gaske farinciki yana nunawa saman fuskarta,duba da sanin babban mutumin data aura. Murmushi sabreen din tayi wanda yakai mata har zuci,musamman data tuna daga rana irin ta yau ta nesanta maamah din da rayuwar qannenta kenan,nesantawa ta har abada "Me zai hana titi?,ban fara fita bane kawai" Ta amsata tana gyara zamanta "To ma sha Allah,ubangiji ya sanya alkhairi,ya bada zaman lafiya ya kade fitina". Bata amsa duka wadannan addu'o'i na titi din ba,sai tace da ita "Alfarma nazo nema titi don girman Allah" Kallonta titi takeyi wani yanayi yana bin fuskarta "Haba sabreen.....haba don Allah,aike din kifi qarfin alfarma......saidai bada umarni kawai" Murmushi ta saki tana girgiza kai,har yanzu suna mata wani madaukakin kallo. "Su huda na kawo miki,inaso kuma ki riqemin su zuwa wani lokaci,don Allah titi ko nan da qofar gida bana so su leqa idan zai yiwu bare sukai ga fita waje.......akwai gagarumar matsala da take tunkararmu gaba daya,akwai masu bibiyar rayuwarsu,ki kulamin dasu don Allah". Sosai maganar ta shigi titi,saita girgiza kai tana fadin "Aiko su din ba jininki bane sabreena sai inda qarfina ya qare......ba abinda bakiyi mana ba,banda ke da Allah ya jefo mana da yanzu bansan a wanne bigire rayuwarmu take kai ba......zan kula miki dasu fiye da yadda kike muradi" "Na gode titi......kina da tsohuwar waya da bakya amfani da ita?" "Banga abun godiya a nan ba,hasalima kamar wajibi na na aikata.....akwai wayata da kika canzamin sanda zamuyi tafiyar nan......bari na dauko miki ita" "Idan zan samu da wata wayar daban zanyi kira" Ta fadi tana qoqarin hada numbers din momma a kanta. Banda tana da kaifin basira da saurin riqe abu ba yadda zata iya hada number wayar momma din,saidai cikin ikon Allah ta hadasu tsaf ta kuma kira zuciyarta na bugawa da fatan ta kira daidai. Bugu uku aka daga,muryar momma ta mamaye speaker din tana amsawa da sautin da yake kama sak dana ummensu,sautin da har tata mutuwar ta risketa ba zata manta dashi ba. "Mom......momma" Sabreen din ta kirata bakinta yana rawa idanunta suna cika fal da hawaye. "Sabreena?.......kun dawo?,yaushe kika dawo?" "Daga ina?" Ta tambayi momma din a mamakance qwallar idonta suna tsagaitawa. "Tafiyar da kukayi mana ke da me gidan.......ko sanda zan koma ai naso haduwa dake dole sai hannun surukarki nabar qannenki.......saboda dole sai passport dinsu ya zama ready.....duk dama dai munyi magana tana ta iya bakin qoqarin ta,kuma kusan kullum sai munyi waya da yaran". Mamaki ya sandarar da sabreen,sai ta bude bakinta a hankali "Momma me ya faru?,ban fahimta ba,ita ta nema ki bata su?" 46 "Eh kusan hakanne,don naso ganinki ban samu ganin naki ba......tafiyar tawa bata shiri bace......abbansu ne rashin lafiya ta taso masa,dole kuma ana buqatata a kusa,a yadda na tsara zan jira passport din nasu da komai ya kammala,amna dole na tafi saboda jinyarsa,saidai ba inda zan barsu don ban aminta da hannun kowa ba. Randa nake wannan tunanin saiga surukarki Allah ya jeho ta. Ita ta roqeni na bata yaran zata sanya mai gidanki yayi magana don a kammala basu komai da wuri,tace kuma zata turosu ko ta kawominsu da kanta,to amma lokacin da nayi tsammani ma sai gashi har ya gota. Kawai abinda yake kwantarmin da hankali duk sanda mukayi waya da yaran alamu suna nunamin basu da matsala ko damuwar komai". Kai kawai sabreen ke jinjinawa tana sake girmama kaidin maamah din. Ta tabbatar ita zata kawo tsaiko a samun fasfunansu,wataqila ma kuwa an samu ta riqe ne taqi gayawa momma din. Tanason ta yiwa momma bayanin da zata fahimceta,amma kuma bataso ta daga mata hankali. Tana ji a jikinta zata iya komai,kuma wannan lokacin kamar wata dama ce da Allah ya ara mata akan maamah din "Momma" "Na'am sabreen" "Komai da kike kallonsa a haka yanzu a zahiri ba'a haka yake ba........abinda zance rayuwarsu tana cikin hadari babba........basa hannunta yanzun suna wani hannun na daban,saidai bana son ki gayawa kowa,don Allah mommma......koda ta kiraki kiyi kaman bakisan abinda yake faruwa ba.......in sha Allah nan da kwanaki kadan zan turosu su biyoki". Shuru momma din tayi tanaji a jikinta ba lafiya "Amma sabreen me yake faruwa?". "Ba wani mummunan abu bane momma,kada ki tashi hankalinki.....kawai dai komai kiyishi kamar bakisan anayi ba" Kai ta jinjina bawai don hankalinta ya kwanta ba sukayi sallama. Tana ajiye wayar ta sabule zobunan hannunta guda biyu na gold,ta kama hannun titi ta zubasu tana kallon idanunta. "Yanzu bani da contact na kowa.....inaso ki saida wannan,ki nema mutumin da ya muku visa na fita india ya yiwa su huda duka su ukun komai,inaso kada su wuce sati biyu a nan don Allah titi". Zobunan ta kalla sannan ta maida dubanta ga sabreen "In sha Allah.....zanyi duk yadda zanyi na miki abinda kikeso". Kai ta jinjina tana jin wata nutsuwa tana saukar mata. Murya ta daga ta kira huda,ta shigo ita daya,abinda ya sanya titi miqewa don basu guri. "Ina wayar hannunki?" Ba musu ta dauki wayar daga kan cinyarta ta miqawa sabreen din. Saita karbeta tana juyata a hannunta. Waya ce me asalin tsada da kyau wanda kusan sai wane da wane. Idanunta ta maida fuskarta tana kallonta "Huda baki dago komai ba?,bakiji komai ba game da matar da aka kira da sunan uwar mijina?" Tayi mata tambayar kai tsaye tanason samun wani abu daya danganci maamah. Shuru hudan tayi,tana qoqarin recalling komai,tun daga ranar farkonsu cikin gidan kawo yau. Siririyar ajiyar zuciya ta sauke,a hankali ta maida dubanta ga sabreen "Inajin kawai batamin ba.....duk kirkin da take gwadana mana sai nakeji jini na da nata kaman bai hadu ba.......sannan yadda take mana kirki kaman ba haka dabi'arta take ga masu aiki qarqashinta ba" Hudan ta fadi abinda da gaske haka takeji a zuciyarta take kuma hasashe. Wani siririn murmushi sabreen ta saki tana saukar da kanta qasa gami da juya wayar hannunta. Anzo daidai gabar da tafiso.....anzo daidai wajen da zata gwadawa maamah shege......anzo daidai gurin da zatayi wasa da hankali da kuma tunaninta kamar yadda mage kanyi da qadangare ko bera a duk sa'ilin da yayi gigi ko kakambar shiga hannunta. Daukewa murmushin fuskarta yayi lokaci guda,ta maida kallonta kan hudan "Ina fata ba wani abu na cutarwa data taba muku......idan kuma akwaishi ko da da mugun kallo ne ina saurarenki". Kai ta girgiza tana kallon addar tata,tanason kuma fahimtar dalilin da yasa taketa mata tambayoyi haka "Babu kwata kwata adda......saidai kawai nidai hankalina ya kasa nutsuwa da ita... Musamman da ya zamana kusan ko yaushe tana mana alqwarin zata kawomu wajenki sai kuma ta gaza cikawa.....har sai da mijinki yazo.....shi yace ta barmu muje". Jinjina kai take tana duban huda dake bayani,fuad ne kenan.......me yasa yace suzo din?,shima akwai yiwuwar yana da nashi boyayyen manufar?. "Kinsan garkuwa tayi daku?,kidnapping a fakaice?" Tambayar ta zowa huda a bazata,ta zaro idanunta waje tana dafe hannunta saman qirjinta. "Kidnapping fa adda?" Kai ya gyada mata gami da lumshe idanunta,sai kuma tace "You are free in sha Allah.....zaku bi momma mali soon......abu daya nakeson na gaya miki ko bayan kun tafi......be smart as much as you can.......ki dinga amfani da kwanyarki da basirarki.....ki kula da nadra da Haneefa,ki zame musu garkuwa kamar yadda na zame muku.....sannan......ki zama mara saurin yarda da mutune,walau maza ko mata,a family yake ko a wajen family......saurin yarda tushen kowacce rushewa ce" Ta qarasa maganar tana nunata da yatsa. Iska ta zuqa sosai sanda take cikin napep din sannan ta furzar da ita waje,tana jinta kamar mutumin daya dauki dutsen dala da gauron dutse yau Allah ya 'yan tashi ya samu saukeshi daga saman kansa. Sakayau take jinta,wani farinciki yana ratsata gami da iskar abun hawa wadda ta manta rabon data ratsata. Ta ware idanu sosai tana kallon titi.....Don yaushe rabonta data fito?,ko fitarta ta qarshe cikin rufaffar mota ne qarqashin kulawar jami'an tsaro. "Sabreena Ahmad AKA MUHSEENA" Sunan da taji an ambata kenan saitin kunnenta. Ko daga bacci ta tashi tasan waye?......wannan wata shaidace kuma stamp ne daya kasance nasa shi kadai. Mashkur....ta gayawa kanta da kanta,don haka ta tattara dukka nutsuwarta da qarfin halinta ta maida sashen da sautin ya fito. Shi dinne,zaune a seat din driver,ya dafe dukka hannuwansa saman steering din motar yana jifanta da wani zazzafan kallo. Duk da yadda haushinta da wutar son daukar fansa ke ruruwa a ruhinsa.......amma hakan bai hana shaidan harbawa zuciyarsa wutar matsananciyar sha'awarta ba. A yadda yake hangen wani lafiyayyen kyau a tattare da skin dinta......wani irin kyau da abaya fatarta bata sameshi ba,sai yakejin burinsa ya ninku zuwa gida biyu,YA DAUKI FANSA sannan kuma YA KASHE QISHIRWAR SHA'AWARTA A RANSA. Dadaddiyar qishirwar data maidashi sakarai kuma shashasha a kanta duk da tarin tsananin wayonsa. "Damn it!" Ya furta da qarfi yana dukan steering din motar tasa gami da cije lips dinsa gami da kashe mata idanu guda daya. Salin alin ta dauke dubanta daga kansa,tana jin wani matsanancin faduwar gaba yana saukar mata. Faduwar gaban da bata taba ji ba a kansa ko akan wani d'a namiji ba idan ka dauke fu'ad din "To ko wannan shine haqqin aure da kowacce mace kejin nauyinsa a kanta?" Ta tambayi kanta da kanta tana jinjina girman abun. Kafin ya sake cewa komai traffic light ya sakesu,motarsu ta riga tasa yin gaba. Cikin mamaki sai ta samu kanta da addu'ar kada ubangiji ya bashi ikon ganinsu har ya biyosu yaga gidan da take,duk da ta sani......gidan su zai wahala ya zama wani boyayyen gida da zai wahalar da za'a iya ganoshi. *MUHAMMAD FU'AD* Basuyi nisa can can ba ya tuna yabar file dinsa a gida,wanda file ne dake da muhimmanci ya dubashi a yau ya tura da bayanan cikinsa ga company din da suka nema sanya hannun jarinsu a kamfanin. Ba kasafai ya fiya son yin alqawari ba tare daya cikashi ba,idan har hakan ta kasance ta tabbas baida yadda zaiyi ne,don haka ya sanya su saddiq sukayi gaba,shi kuma suka juya da wasu motocin suna dawowa gidan. Wuri wuri zuwaira tayi ta shiga raba idanu sanda taji dirin shigowar motocin nasa harabar gidan. Raba idanu ta shiga yi sannan ta furta kalmar "Na shiga uku!" Bayan ta tuna gargadin da yayi mata a ranar daya fara ganinta. Yadda tasan halinsa ta kuma haddaceshi bata haddace fuskarsa haka ba,ta tabbatar yazo ya sameta a sassan kamar yadda ya gargadeta shan ruwanta a gidan ya qare. Wani abu guda daya da bata qaunar ya faru......zaman gidan yafi mata zaman ko ina......zaman gidan cike kuma yake da 'yanci,ba kyara ba tsangwama,hakanan ba nauyayen aikace aikace a cikinsa,sabanin gidan maamah din da yake cike da tsarabe tsarabe kala kala. Wuf tayi ta miqe tana dosar qofar da zata sadata da sassansu kamar zata ci da baka,cikin ranta cike fal da Allah ya qarawa laila tare da fatan ubangiji ya hadata dashi yaci zarafinta har fiye da tunaninta taga yadda abun zai kaya. Da nutsuwar nan tasa ya shigo cikin falon,idanunsa suna kan inda ta tsaya a dazun sannan ta waiwaya tana komawa ciki. Ya janye lumsassun idanunsa yana wucewa parlor na biyu,daga nan ya doshi qofar da zata sadashi da hallway da kuma stairs dinsa. Saurin ja yayi da baya kaman yadda itama taja da baya da sauri. Ya zuba mata idanu yayin da ita kuma kwarjininsa yaso bugar da ita. Bata shirya ba amma sai gata tana rusunawa gami da gaidashi "Barka da safiya hamma.....ya aiki?" "Kece laila?" Ya tambayeta yana dinke girarsa tsaf saboda yadda yaga abun ya masa wani iri. Ta yaya zata ratsa privacy dinsu ta shigo har nan wajen?,wani irin rashin hankali ne da ita matar gidan zata bari haka ya faru?. Shi din wani irin mutum ne me tsananin son privacy,kamar yadda yake da iyakoki akan komai daya shafi rayuwarsa.....kuma kowanne mutum da nashi iyakar. Murmushi ta saki tana wani karyar da wuya gami da rolling idanunta a kansa "Eh hamma.....nice.....baka gane ni ba?,nazo ne duba.....ammm.....ammm sabreen,maamah nason magana da ita da gaggawa,so kuma unfortunately sai na duba ko ina na gidan amma babu ita.....infact ma ta fita.....". Banbarakwai yaji maganar kamar da wani yare daban take magana. Ta fita?,zuwa ina kenan?,sannan da izinin waye ta fita?. Ajiye duka maganganun yayi gefe guda yana dubanta "What I have told you tun ranar farko?.....so ki hada kayanki kibar gidan nan" Yayi maganar da murya me kaushi dake cike da zallar umarni. Hukuncin ya daketa so sai hakanan ya mata tsanani,iya ganinsa data sakeyi yanzu ya sake tada tsimin soyayyarsa a zuciyarta,saita dubeshi a rikice "Amma hamma....maamah ce....." "Arguing won't help the situation" Ya fada da wani irin yanayi maras hargagi saidai kuma me ban tsoro ne a idanuwanta. Sum sum da wani irin sagaggiyar gwiwa tsoro da bacin rai ta miqe tana fita daga wajen. Ya bita da wani irin matsiyacin kallo,sannan yaja tsaki kamar zai tsinke harshensa. Har ya taka stair case din sai kuma ya dakata. Ta fita bata gidan?,maganar ta dawo masa fes cikin kansa. Juyawa yayi don tabbatar da abinda lailan ta fada,ya fara bincike gidan guri guri. Kaf ya gama duba ko ina a gidan,ya kuma tabbatar bata nan din. Wani wutar fushi yaji tana ruruwa cikin ransa,yana so yaje ya saukewa duka Securities na gidan,amna kuma wata zuciyar na gaya masa MARTABAR AURE koda sunanta MATARKA KADAI A FATAR BAKI. Samun kansa yayi da bin lafiyar daya daga cikin kujerun parlor din farko,yayi relaxing kawai a ciki yana jin yadda jijiyoyin kansa suke harbawa,ba abinda zuciya bata raya masa ba,ina ta tafi?,wajen su waye taje?. "Da igiyar aure na?" Ya tambayi kansa da kansa yana jin yadda zuciyarsa yadda take tafasa. Bai taba tunanin akwai wata diya mace da zai bari tayi masa wasa da igiyoyin aurensa da ya biya sadakin daya nemo da guminsa ya bayar ba,kai koda sadakarta aka bashi muddin da sunan muhammadu fu'ad jikan jadda aka daura bazai taba bari wani abu ya gilmawa mutuncin igiyarsa ba......idan shi ya warwareta tofa wannan daya. Ba kasafai ake barin napep shiga unguwar ba,wannan ya sanyata dole ta sauka daga baya ta sallameshi,sannan ta fara takawa cikin nutsatsen takunta zuwa street din nasu. Duk gidan dake da security a wajen suna ganinta sai taga suna miqo gaisuwa da wani irin respect,abun sai ya shiga bata mamaki ita kanta. Wai har girma da matsayinsa yakai wannan?,sannu sannu sai taga alamun mamaki bisa fuskar duk wanda ya ganta tana takowa da qafafunta. A hankali taji alamun tafiyar tayar mota daga bayanta. Bata waiwaya ba,don tun can dama ita bame damuwa da abinda bai shafeta bane 47 _Daga abdullahi dan abbas R.A yace,Lokacin da aliyyu R.A ya auri nana fadima,sai manzon Allah S A W yace"ka bata wani abu(a matsayin sadakinta),sai sayyadina Aliyyu yace "ba komai a wajena" Sai manzan Allah S A W yace "ina sulkenka?"_ "Ameenatu" Taji muryar nan dai ta dazu tayi kiranta. Sai da taja numfashi sosai tana son danne bugun da zuciyarta keyi sannan ta waiwaya inda ya daidaita motarsa saitinta,yana zaune kusa da window yana murxa steering hankali kwance fuskarsa shimfide da wani shu'umin murmushi. "Na rantse wannan karon ba zaki sha ba......na miki wannan alqawarin muddin na haifu cikin uwata da ubana......lallai saina maida sha'awata a kanki......sai kuma na bankadawa duniya wacece ke bayan na maido kudadena cikin dukiyata......ki rubuta ki ajiye" Daga haka yayi saluting nata,sannan ya taka motar da gudu yana wuceta. Bata fasa takawa tana nufar gida ba,kamar yadda bata fasa bin bayan motarsa da kallo ba har ya qurewa street din nasu. Wata mahaukaciyar fargaba tana ratsa zuciyarta,sunan mashkur tare da cikakken sanin wayeshi yana gewa tunaninta,a haka ta isa qofar gidan,ta kuma yi tsaye tana duban dogayen katangun gidan kamar me karantar ilimin zanen gidaje. Tana wassafa yadda zai iya tsallake wadannan dogayen katangun mansion House din......tana qiyasta ta yaya zai iya wuce wadannan securities din da samudawan dake tsaron kowacce kusurwa ta gidan?. Tsaron gidan kadai ya dan sanyawa zuciyarta nutsuwa.....saidai kuma bai kore fargaba ko kuma ya mantar da ita wanene ASALIN MASHKUR BA. Gangar hankalinta bata dawo jikinta ba sai data sanya qafafunta cikin gidan,idanuwanta kuma sukayi mata arba luxury cars dinsa dinnan dake ajiye a parking lot na gidan. Sai yanzu ta tuna bata nema izinin kowa ba sanda zata fita,don sam ta manta hakan yana cikin wata doka dake kan kowacce macen aure.....baya ga haka.....a lokacin ba abinda take iya tunawa illa hanyoyin da zata nesanta rayuwarsu da maamah din. Da confidence din ba lallai su hadu ba har ta wuce daki.....ba lallai ma yasan bata a cikin gidan ba ta tura glass door din parlor din tana sanya qafafunta. Da bude qofar da haduwar idanuwansu lokaci guda ya faru. Iya kallon data gani cikin rusunannun idanuwansa sun bata wata fargaba da bata taba jinta akan kowa da komai ba. Dakiya ta aro ta azawa ranta,tana jin a ranta a yanzu daidai take da kowa a cikinsu.....ko shi ko mamarsa. Tana jin lokaci bijirewa dukka wani sharuda nasu yazo,tana jin abinda ya rage mata biyu ne......ta samu tabbacin fitarsu zuwa mali a sannan takejin zaman wannan qallagaggen gidan dama me gidan gaba daya ya qare mata. Cikin dakiya da basarwa taci gaba da takowa kaman bataga kowa zaune a parlor din. Tsaf ya gama karanta da kuma fahimtar abinda take shirin aikatawa. Ba za'a fishi sanin miskilanci take taken miskili da kowacce dabi'a tasa ba,sai ya dauke kai kaman bai damu da takunta ba,zuciyarsa na sake matsewa,ransa kuma yana qara baci har zuwa sanda ta raba tsakiyar falon. Ba zato ba tsammani ta tsinceshi a gabanta. Tsaiwarsa yayi mugun dab da ita,hucin fitar numfashinsa da wani irin dumi da yake bayyanar da bacin rai da zuciyarsa ke ciki yana sauka saman goshinta. Motsawa tayi da nufin ja baya don bata tazara a tsakaninsu qirjinta na wani irin bugawa,saidai da tsananin zafin naman nan nasa ya cafki hannunta yana matsawa da kyau "Daga ina kike?!,ina kika fita?,gurin waye kika je?" Ya tambaya a jere cikin tsawar data ratsa dodon kunnenta har sai data runtse idanunta. Tattara dukka qarfinta tayi ta sabule hannunta daga nasa,wanda ta samu sauqin hakanne saboda banguls din hannunta ya riqe saita zame ta barshi dasu,saidai ko taku biyu batayi ba ya rufo mata baya,sai ya zamana tana tafiya da baya da baya,shi kuma yana maida qafarsa kowanne gurbi data cira qafartata. Kowanne taku guda daya sai qwayar idanunta sun gauraya da nashi. Abinda take gani cikin idonsa batasan wanne iri bane......wani yanayi ne da bazata iya fasaltashi ba. Yana sake kunsatota yana sake maimaita mata tambayoyin da suke sake razanata,bata ankara ba taji ta bugi bango,tabbacin kowanne space ya qare mata kenan,sai tayi cak sanda ya iso dab da ita,cikken motsi idan tayi yana iya sata ta kasance cikin jikinsa. "Gurin wa kika je?,me kuma kikaje yi nace!" "Ban sani ba" Ta fada da rawar murya tana qoqarin daidata mode dinta. Ko kusa ko alama bata tanadi amsar da zata bashi ba.....shi kuma ya matsa mata da tambaya.....tambayar da ba abinda take mata sai qara fusatata......GURIN WA KIKA JE?,ME KIKAYI?,idan ya fada din sai taji kamar ha debo garwashin wuta ya watsawa sassan jikinta ne. Ba abinda yake tuna mata sai mummunar kalmar yawan mutane musamman na cikin gidansu suke jifanta da ita.....kalmar da koda ta nuna ta shanyeta tana iya hana idanunta bacci da wani matsanancin fushi da bacin rai.....shima irinta yakeso ya ara ya yafa yayi aiki da ita a kanta?,batajin kunnuwanta zasu iya jurar ci gaba da jin ana jifanta da kalmar da bata da masaniyar komai a kanta. Hannuwansa ya dunqule waje guda yanason hana kansa marinta da zuciyarsa keda muradin yi. Bayaso yakai hannunsa jikinta......baya so ta zama mace ta farko daya fara mari duk kuwa da yanajin ta cancanci haka. "Karki bari nayita maimaita maganata......ina kika fita ba tare da izinina ba?....wajen wa kika je?!!!!" Yayi zancan da wani irin qaraji daya sanyata curewa waje guda,kowanne sashe na jikinta ya dauki rawa "Banje wajen kowa ba.....ni ba wajen wanda naje" "....You're going to regret messing with me,for the last time....ina kikaje?" Ya sake tambayar yana sanya hannuwansa duka biyun dake a dunqule ya daki bangon da take maqale a jiki ta saitin kunnuwanta. Abinda ya sake gigitata kenan ta saka hannuwanta duka biyun tana toshe kunnuwanta gami da rruntse idanunta. Zuwa sannan kowacce jarumta dake jikinta tabi ruwa.....ba abinda ya rage mata sai rauni daya narke zuwa kuka. Cikin qasa da second biyu ta tsinci hannuwan nata jikin nata hannun dake toshe da kunnenta yana saukesu,da wani irin taushi da sanyin murya taji yana fadin "Is okay......wanne irin matsoraciya ce ke?.enough,stop crying please" Bata qara tuna komai ba ta tsinci kanta saman faffadan qirjinsa,ya sanya hannunsa daya ya lullube bayanta,daya hannun kuma yana shafa gadon bayan nata da irin salon da uwa kanyi don lallashin jaririnta. Wani sassanyan qamshi dake ratsowa daga qirjinsa da kuma kowanne sashe na jikinsa ya cika hancinta da wani irin sanyi daya soma qoqarin daidaita yanayinta. Saidai hakan ya gaza samuwa,don qarasa rudata yayi,daga yadda kunnuwanta ke iya jin yadda zuciyarsa take bugawa kadai ya tabbatar mata fusatarsa ta gaske ce......amma me ya sanyashi sauya yanayi haka cikin qanqanin lokaci tamkar wahainiya?. To kodai yana da boyayyun aljanu da suke sauyashi haka da sauri?. Bata gama wannan tunanin ba muryar ma'u ta zame mata amsa "Ina neman afuwa ranka ya dade.....ayimin afuwa" Ta furta da tsananin kunya tana sadda kanta qasa. Bata taba tunanin zatazo ta samesu haka dab da juna ba,kwata kwata ma batayi tunanin suna nan ba,tasan me gidan dai ya fita......dawowar da tayi kuma tazo dubawa amna ko ta dawo?,don sun hadu ta daya qofar sai kawai ta shiga sassanta da taji sabreen din bata nan. Kai kawai ya gyada yana ci gaba da shafa bayanta kadan kadan "Hajiya amna ce tace nazo na duba kota dawo......" "......ta dawo.....amma batajin dadi,kice ta qaraso" Da sauri ma'u ta amsa ta juya tana ficewa a gaggauce. Kaman yana jira ne ma'u din ta fita ya saka hannunsa ya tureta daga jikinsa. Banda yana kusa da bangon daya bata kariya ba abinda zai hanata zubewa qasa. Da wani fusataccen kallo yake dubanta. "Kada ki dauka na yarda ne da abinda kika gayamin......muddin na bincika na samu wani abu na daban saina miki mafi munin hukuncin da baki taba tunani ba......hakanan duk ranar da kika qara gangancin fita koda qofar gidan nan ne ba tare da izinina ba......saikinyi dana sanin sani na........nan din gida ne da aka gina da tsaftatacciyar dukiya ta halas.....ba bariki bane ba ba kuma hotel ko gidan karuwai ba" Daga haka ya juya yana daukan file dinsa dake ajiye saman daya daga cikin kujerun falon yana ficewa da sassarfa. Wani irin kuka ne yakeson qwace mata amma tana hana kanta,don idan har kunnuwanta sun jiye mata daidai amna na gidan,kuma zata iya iskota koda wanne lokaci,dole ta tattaro dukka wani bacin rai tana hadiyeshi,saidai kuma abinda takeji yafi qarfin abinda zuciyarta zata iya dauka,sai bacin ranta ya zabi fita ta hanyar fitar hawaye daga idanunta zuwa saman fuskarta,ta lallaba tana neman kujera daya ta zauna a kai tana dafe da kanta. "Oh god........ damn it....." Abinda ya dinga maimaitawa kenan cikin mota yana saka yatsunsa cikin sumar kansa. Ya manta yaushe ne lokaci na qarshe daya fusata irin haka.....yaushe rabon da yaji zallar bacin rai irin wannan dake ratsa kowanne sassa na jikinsa. Ya alaqanta hakan da tozarta igiyar aure da yake shirin faruwa. Sai ya samu kansa da blaming kansa,me yasa zai daga hankalinsa har haka?,ai duk wanda ya siya rariya yasan zata zubda ruwa. Ransa yaji yana qara baci,sai ya yiwa driver magana ya qara speed na motor din. 48 _An karbo daga abu hurairah Allah ya qara yarda dashi yace,manzon Allah S A W yace,idan miji ya kira matarsa zuwa shimfida taqi zuwa,mala'iku zasuyita la'antarta har gari ya waye_ *_qarqashin wannan hadisin akwai qarin haske,idan a wannan qin da tayi kuma ta samu ciki koda ta rasu wajen haihuwa wasu malamai suna ganin bata samu wannan shahadar da mace me naquda ke samu ba idan ta rasu_* *MAAMAH* Tunda ta cewa zuwaira taje ta duba mata su taci gaba da kiran wayarta ba qaqqautawa don ta matsu taji feedback,saidai kuma shuru ba'a picking wayar. Saita koma kiran wayar laila ita dinma duka sammakal. Kamar ta dora hannuwanta akai tayita rusa ihu haka taji,ta tsinewa zuwaira da laila a ranta batasan adadi ba "Dukkaninku baku da amfani" Ta fada da fushi,sai taji kamar ba zata iya zama ba....wannan karon zata tafi gidan fuad da kanta ne ta dubo meke faruwa ba tare da damuwa da komai ba. Tana taka qafarta kiran zuwaira ya shigo,tayi qoqarin hadiye fushinta tana fatar samun feedback me dadi,saidai amsar da zuwaira ta bata ya kusa sanyata zubewa qasa warwas "Bata gidan ita kanta.....kuma akan idanuna ta dawo ita kadai". Iya haka kadai ya bawa maamah amsar abinda taketa zulumin ya faru. Ta kwashesu,ta tseratar dasu,amma dai bata sare ba,tana da sauran hope,don haka kai tsaye ta fara kiran number huda. Kiran duniya computer ta gaya mata ta kuma jaddada mata wannan layin a kashe yake. Ta laluba wayarta kaf ta rasa number wayar bokanta tana me mancewa da cewa mutumin baya riqe waya,yo mutumin dake rayuwar tsakiyar dajin Allah ina gaya service ma bare waya ta dameshi?,mutumin da yake kewaye da aljanu,suke kai masa saqo kuma ku amso masa ko daga ina ne?,me zaiyi da waya?. Hajja harira ce ta fado mata,ba bata lokaci ta danna number dinta tahau kira. *Hajja harira* Tun fitar laila bata iya tashi daga wajen ba,idan tace ta qulla tunani sama da dubu da kwancesu tsaf a wajen ba zatayi musu ba. Duk wani tunaninta idan yaje ya dawo a waje daya yake cakewa,tun tana neman qaryata abinda take zargi har zuciyarta ta gama yin ittifaqin amsar dai itace "Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un" Ta furta da wani matsanancin tashin hankali. Tayi imani muddin abinda take zargi ne ya tabbata.....to lallai laila zata qare rayuwarta kaf wajen bautar maamah...... Asiri ne da bashi da makari sai mutuwa.....yaci uban bita zaizai,yafi uban tace saidai kafin tace. Ita mariya zata yiwa haka?,wannan shine sakamakon alkhairin da ita tayi mata?. Kamar tasan itace a gaban tunaninta saiga kiranta ya shigo. Kamar kada ta daga amma kuma wani tunani daya darsu a ranta ya sanyata gyaran murya ta daidaita muryarta sannan ta daga din. "Al'amura kamar suna shirin kwabewa hajja.....ina tsoron kada zancan mutumin nan ya fara tabbata......ki taimakeni hajja". Maamah ta fada da tsananin damuwa,damuwar data saka hajja taji wani bangaren na tata damuwar da tashin hankalin suna samun sassauci.....ko banza ba ita kadai ke cikin damuwa ba......ba kuma ita kadai zata ci gaba da zama a cikinta ba,taci alwashin dukka yadda zatayi zata yi don maamah taci gaba da tabbata cikin damuwar ta,waye ya gaya mata yaro yana wasa da kan maciji koda kuwa ya rasa abun wasa?. Yanayinta ta daidaita don yayi dai dai da yadda maamah zataso taji,tana mamakin zallar rainin hankali irin nata. Bayan mummunar sakayyar da tayi mata,kuma wai ta nemeta da tata matsalar tamkar ma batasan me ya faru ba?. "Me yake faruwa?" "Garkuwata ta subucemin......daga yanzu zuwa kowanne lokaci zan iya fuskantar barazana daga wajen abun hari na,kowanne hope nawa kuma ya subuce hajja.....meye abunyi?" Ta qarasa maganar da sigar tambaya cike da damuwa. Iska hajja ta furzar tana dan bubbuga tafin qafarta kadan kadan,a nutse tace da ita. "Bani lokaci mariya nayi tunani......mintuna kadan nake buqata". Jikinta a sanyaye ta amsa mata suna katse wayar su dukka biyun. Wayarta take dan bugawa cikin tafin hannunta cikin salo na tunani. Mariya shegen kai ce,tana da nata matsanancin wayon da kai da kake rayuwa da ita kayi kadan ka fahimci komai idan ba ita taso ba.......saidai kuma a wannan yanayin da ake ciki mariya tana tafin hannunta ne. Bata isa tayi wani motsi cikakke ba ba tare da ita ba,itace ginshiqin.....itace kuma madogarar. To shin batasan abinda tayi mata bane?,batasan me ya faru ba?,ko tsananin iya bariki ce kawai?. "Inaso na samu tabbaci" Ta furta tana daukar wayarta data aje tun daxun ta sake lalubar number maamah din. Bugu daya tak ta daga,ta sanya wayar a kunnenta tana kiran sunan hajja. "Duk abinda zaka daukoshi ko ka matso dashi don biyan buqatarka......kuma ya gaza yin wannan aikin sai nakega bashi da wani amfani,kau dashi kawai zaifi.....me zai hana ta gusa daga rayuwar fuad tun kafin matsalolin da boka ya baki a dunqule su fara bayyana har sufi qarfin shawowarki?....ga laila nan?,umarni na da naki sune zasu zama abun binta,a azata a bigiren da wannan ke kai,nayi Imani da laila......tabbas ba zata sabawa tsarinmu ba......sirrinmu kuma a lullube". Nauyi maamah taji maganar tayi mata,sannan sam bataji maganar ta kama hankalinta ba. Har cikin jininta da zuciyarta takejin laila bata mata ba,kwata kwata bata dace da wannan aikin ba,bata dace ma ta zama matarsa ba koda na minti guda ne kuwa. Tasan wacce hajja farin sani,tana tunanin ita ko yaronta zasu kubuta daga ayyukanta ne?,sai ta girgiza kai a fili tana jin abun bai kama hankalinta ba. To amma dole sai tabi ta takatsantsan kafin ta fahimtar da hajja din,tafi kowa sanin hajjan akan laila bata dagawa kowa da komai qafa. "Aah fa hajja harira,laila ni dake duka 'yarmu ce......ba zamj jefata cikin wannan risk din da wahalar ba......qyale bare dai,wanda idan ya sabawa tsarinmu kowanne mataki zai iya fadawa kansa........kamar yadda itama wannan din MUMMUNAN SAKAMAKO na rantse miki da Allah zai yita bibiyarta......ba zan qyaleta ba,sai na banbance mata tsakanin aya da tsakuwa!" . Turqashi!.....hajja ta fada qasan ranta,kai tsaye a bayyana ko a kaikaice maamah bata qaunar laila ta kafa tarihin zama matar muhammad me jadda.....wannan shine amsar tambayarta kai tsaye idan aka cire kauce kauce. "Ke yanzun wanne shiri ne na gaba kike ganin ya kamata muyi?" Ta mata tambayar tana relaxing kanta don samun bakin zaren daga inda zata dasa nata aikin. "Ki bari tukunna na samu nutsuwa daga wannan,abubuwa su hau kan saiti,zaki ganewa idanuwanki ba tare da nace dake komai ba". Ta fadi mata kaman yadda ta saba. Tana da boye duk wani shiri nata,zai wahala tana kan shiri ka sani,ko a baya wannan ne ya zama SILA da sanadin da LAILA ta shiga DUNIYAR lissafinta,qila data tsaya neman fashin baqi wajen boka kamar yadda hajja taso suji......ba shakka da qila yanzun haka laila bata fada wannan BAQAR MASIFAR ba....dukka hajja ke wannan tunanin cikin ranta tana jin wani bacin rai yana taso mata. Hajjan ta bude baki zatace wani abu sautin kukan laila ya mamayi kunnuwanta daga cikin wayar. Wani abu ya daketa,tayi shuru tana sauraren tambayar da maamah keyi mata kafin kiran ya yanke. "Tashin hankali!" Ta fada a sarari tana miqewa tsaye,ji take kamar ta wuce kai tsaye gidan maamah amma wata zuciyar na jan kunnenta "Sai kinyi kamar baki sani ba......sai kinyi kamar baki fahimci komai ba,saikin maida komai ba komai ba". Wadannan maganganun suka sanyata rusuna ta koma ta zauna wuta naci gaba da balbala a zuciyarta. Daidai sannan nafessa ta shigo da mopper da broomstick tare da sallama a sanyaye cikin girmamawa. "Ubanme kika shigo kiyimin?". Kai ta sunkunyar "Kiyi haquri,haidar ne ya tashi da zazzabin haqori yau shi yasa ban shigo sharar da wuri ba". Duk da jikanta ne bata tsaya ta nuna kulawa ko alhinin komai ba,hasalima bata fahimci gaya mata take baida lafiya ba yaron,sai ta daka mata tsawa tana fadin " Sharar da bakiyita dazu ba sai yanzu ko?,baqar munafuka,fita ki bani waje". Tashi sosai hankalim nafeesa yayi,take idanunta suka tara ruwan hawaye,tana tsoron me zata gayawa d'anta a kanta idan ya dawo,tanason aurenta batason ta kashe mata shi,wannan ya sanya ta sulale tana tsugunnawa ta soma mata magiya tana bata haquri "Ki tashi bani waje kafin na rufeki da duka,sharar ce nace banaso ko ana dole?" A nan ta fahimci bawai iya rashin sharar bane kawai da ba'ayi ba ya sanyata haka,akwai wani abu na daban da ya bata mata rai,wannan ya bata sassauci sai ta miqe tana sake bata haquri ta bude qofar ta fita gami da rufe mata. A qasan ranta tana tafe tana addu'ar "Ubangiji ka qara mata damuwa fiye da damuwoyin data sanyawa zukatanmu.......ya rabbi ka shagaltar da ita da damuwarta ta yadda zata zame mana mu kuma hutun da bamu taba samunsa cikin gidajen mazajenmu ba". 49 _Daga abi sa'eed RA yace:manzan Allah S A W yace; "idan dayanku yazo masallaci,ya duba takalminsa,idan akwai qazanta ya shareta ya kawar da ita daga jiki,yayi sallah da takalminsa_ *_halal ne sallah da takalmi a qafa,na haramci a ciki muddin ba najasa ko dauda a jiki_* 49 Ta furta har tsakiyar ranta tana jin ciwon bautar da suke ciki,wadda basusan ranar fitarsu a ciki din ba,sunfi kyautata zaton wataqila sai ranar da surukar tasu ta kwanta dama. Ajiye wayar maamah tayi a gefanta tana duban laila da hawaye ya yiwa fuskarta shabe shabe "Lafiya laila?,me yake faruwa?" Ta maimaita tambayar tana riqe hannunta "Hamma fu'ad ne maamah......ya koreni". Fuska ta ya mutse tana duban lailan,tashin hankalin da take ciki a yanzun bata jin yakai korar laila daga gidan fu'ad,duk kuwa da cewa hakan da yayi taji ya tabata ya kuma qara bacin ran da takeji a ranta. Ya nuna bata isa ba kenan kamar yadda ta saba.....amma yanzun ba shine abinda ya kamata ta damu dashi ba.....tanason tasan ina yaran?.......ina suka shige?,meye manufar yarinyar?,meye takunta na gaba?. "Kina da buqatar ki koma gidan?" Maamah tayi mata tambayar kai tsaye,don son tabbatar da maganar da sukayi da hajja a yanzun. Shuru lailan tayi,tana jin tamkar kowanne tsari na zuciyarta da kuma tunani na qwaqwalwarta ya birkice,tsare tsarenta......burikanta dama duk wani abu dake gabanta sai takejin yana sauya muhalli. Tanason fu'ad sosai......tana kuma jin soyayyarsa.......amma sai takejin zama da maamah yafi mata zama da fu'ad dadi......hakanan ko me maamah ta furta shine umarninta,to tabbas zata iya aikatashi komai tsanani da tsaurinsa. "Inason hamma fu'ad sosai,inaso na aureshi.......kuma hajja tayimin alqawarin sai na aureshi....." Maganar sai ta zowa maamah banbarakwai,tayi mata saukar ba zata,ta xubawa laila idanu tana mamakin furucinta tare da tantamar lafiyar qwaqwalwar laila din. "Tayi miki alqawari?,yaushe kenan laila?" Maamah data tattara dukka hankalinta akan lailan ta fada cikin tsananin mutuwa da kuma sanyin jiki. "Tun sanda ake shirin auren hamma fu'ad.....ta kaini gidan na zauna don na karanceshi tsaf,sannan ta bani ayyukan da zan bashi yaci saboda jawo da hankalinsa kaina da kuma siyan soyayyata......wanda daga qarshe takeson ya dawo hannunta gaba daya". " Innalillahi wa inna ilaihi raji'un" Maamah ta fada tana jin saman kujerar yayi mata tudu da yawa,ba zata iya zama a kai ba duk da laushinta,sai ta sulale ta zauna sosai a qasa. Ta sake zubawa laila idanu sosai maganar na ratsata,amma kuma tana cike da tantama da tunanin cikakkiyar lafiyar kwanyar laila. "Tabbas laila ta fara shaye shaye" Shine abinda maamah ke ayyanawa a ranta. Ba yadda za'ayi hankalin laila daidai......lafiyarta kuma qalau ta dauki babban sirri da labarin cikakkiyar cin amana irin wannan ta gaya mata. "Don Allah kada kiyi fushi dani.....kome kike buqata zan miki maamah" Laila ta fada alamu na bayyana kuka nason qwace mata. Al'amarin ya sake jefa maamah a madaukakin mamaki "Me kikeso in sake baki labari?" Laila da gabanta keta faduwa cikin matsanancin tsoron kada ta batawa maamah ta fada tana durqusawa a gabanta. Mamaki ya sake kashe maamah,ta sake saka idanu ko zataga wani abu na tabin hankali ko hauka tattare da laila,saidai ko kadan bataga wannan ba illa tsantsar biyayya da faranta rai da takeso ta yiwa maamah din. "Ki nutsu mariya.....ki nutsu,makashinka tabarmarka......makashinka yana tare da kai" Wata zuciyar ta ankarar da ita,wannan ya sanya ta aje mamakinta da tunaninta meke faruwa?,ta maida hankalinta ga laila "Tashi ki zauna sosai muyi magana" Cikin hanzari ta miqe ta koma inda saitin inda maamah ke nuna mata ta zauna. "Me yasa kika yanke hukuncin gayamin sirrinku ke da mamarki?" Ta tambayeta da matsanancin mamaki. "Saboda ya zamemin dole na inyi miki biyayya.....inajin cewa ke din kamar uwargijiyata ce.....ni kuma baiwarki,inajin kamar dama can an halicceni ne don na miki biyayya,inajin komai zai iya samu na muddin ban miki biyayya ba......burina na mutu ina miki biyayya.....burina na mutu ina bauta miki". Ta qarashe maganar da zallar gaskiya da kuma yanayin da yake nuna cewa da gaske take furta maganar dake cikin ranta din. Kowacce tsiga ta jikin maamah sai data zuba,wannan shine kwatankwacin abinda take buri,take fata take kuma mafarkin taji ta kuma gani daga wajen fu'ad......ya akayi haka ta kasance akan laila. "Laila......akwai abinda aka dafawa fu'ad a gidansa baici ba ke kika ci?" Ta jefa mata tambayar da zallar kokwanto a ranta. Kai tsaye ta gyada mata kai tana dubanta "Eh.....kwana hudu da suka wuce,naci abincin dare a dining dinsu" "Shikenan!" Maamah ta furta tana runtse idonta,tayi tsam da ranta bata iya cewa komai ba. Tsahon wasu sakanni tana nazari a zuciyarta,kafin kuma a hankali taji kowanne tashin hankali yana sulalewa daga zuciyartata. Idanunta ta ware akan lailan "Meye shirinku a kaina.....meye shirinku akan fu'ad?" Tambayar data yiwa laila kenan tana da yaqinin da tabbacin zata gaya mata komai tiryan tiryan. Shuru maamah tayi tana biye da laila din har ta gama kwashe mata bayanin komai. Ba bayanin yadda lailan ta zayyane mata komai bane yafi daga mata hankali ba,qulli da tuggun da hajja ta shirya qarqashin nata shirin shine abu mafi tsoratarwa da razanarwa a wajenta. Don baje sirrinsu tasan zata samu information akan dukkanin abinda ya shafi hajja sama da abinda laila ta gaya mata ma a yanzu.....muddin wannan hadadden tanadin data yiwa fu'ad ne ya isa cikin laila.....to ko kashi lailan zatayi kuma take da buqatar ta shaida mata kafin ta yishi.....lallai ko bayan gida zai kashe laila ba zatayi ba sai da yarjewar maamah. Take dukkanin wani alhini da fargabar cin abincin da laila tayi ya fice daga zuciyar maamah. Baqincikinta daya asarar data jawo mata,gagarumin shirinta daya baci,wanda ta kashewa maquden kudade masu yawan gaske don ta samu fu'ad a hannunta,yanxu samun laila me zai tsinana mata?,banda kaya da zata zame mata?. Idan akwai riba guda da zata samu itace......ribar nunawa hajja kuskurenta na ha'intar qauna da aminci da tayi "Lallai zan mulki laila ko don na nunawa hajja itadin qanqanuwar maciyar amana ce.....zan mulki laila a gaban idanunta.....zan kuma bautar da ita yadda take bautar da d'iyoyin mutane cikin gidanta". Duk da takaici tashin hankali da baqinciki daya cika mata zuciya amma saita dubi laila da dan murmushi "Zaki zauna dani?" Da sauri ta daga kanta tana jin kamar an mata rahama ne "Zan zauna.....zan zauna dake maamah.....hakan yafimin komai dadi a duniya" "Da kyau" Ta fada a hankali,dan daga murya tayi sannan ta kira daya daga cikin masu aikinta na gidan tace "A bata daki" Ta bisu da kallo sai data tabbatar sun fice a falon sannan ta maida hankalinta cikin jikinta, Iska me zafi ta furzar tana lula kanta cikin duniyar tufka da warwara......babu babban target dinta a yanzu haka idan ba sabreen ba. Bata gidan ta fita.....shine abinda ta yita nanatawa tana shafa lips dinta da yatsantsa. Da sauri kaman wadda aka tsikara ta jawo wayarta,ta tafi kai tsaye izuwa ma'ajiyar lambobi ta zarce can qasa. A jere numbers din nasu suke,saidai kuma tayita kai kawo akan waye zata kira a cikinsu?,waye yafi zafin aiki?. Cak idanunta ya tsaya akan wata number da aka rubuta sunan HANZARI bata tsaya jinkiri ba ta danna kan number ta tura gaba izuwa kira. Bugu daya tak aka daga,da wata iriyar birktacciyar murya ake fadin "Allah yabar mana ke uwar dakina maganin kuka na". Wannan kirarin nasa yana fasa mata kai ainun,kuma ko a yanzun shi kadai ya bata tarin qwarin gwiwa "Nayi missing target hanzari.......ka shirya ko da kowanne lokaci zaka iya jin kirana......idan kiran kuma ya tabbata......babban aiki nake da buqatar ayimin wanda daga shi bani da sauran haufi ko matsala" "An gama uwar dakina" Ya fada da qatuwar muryarsa,bata jira komai ba ta kashe kiran,ta kuma maida akalar kiran nata zuwa ga number huda. Abu daya dai ake sake gaya mata,layin a kashe yake,saita saita lokutan da zataci gaba da kira daga nan har zuwa awa ashirin da hudu,ta aje wayar ta kuma shiga tunanin meye abunyi na gaba?. *MASHKUR* A hankali ya sake gilmawa da motar ta gaban gidan,ba kuma wai don yana da wani abunyi ba ko kuma lalura ke sanyashi wannan zirga zirgar da yakeyi ba......aah,yana yine saboda nazartar gidan da kuma dukka wani kai kawo na jama'ar gidan dama ma'aikatan dake aiki cikin gidan daga dare har rana. Wadanda suke shifting da kuma wadanda zamansu kenan. Yayi gaba,amma sai yaci gaba da kallon gidan ta rearview mirror yana kada kansa a hankali. Babba duk inda yake babba ne,gidan na daya daga cikin dream house dinsa daya jima yana tunanin idan har ya samu yadda yakeso a shekaru goma masu zuwa zaya mallaki irinsa. Hannunsa ya sanya ya daki steering din motar yana jin wani zafi cikin ransa. Yarinyar tasha dashi da yawa a rayuwa,banda wani abu daya rinjayi zuciyarsa tabbas plan A dinsa a yanzu shine zai zama plan B,plan B kuma shine a plan A,to amma duka wannan bazaiyi aiki ba......yana ganin gwara ya fara diban ganimar tukunna,idan yaso ko meye zai faru daga baya me sauqi ne. "Ina fata ka gama kallon komai?" Yayi magana da mutumin dake zaune a back seat wanda zai wahala ka iya fahimtar da mutum a gurin. Kai ya jinjina yana motsa system din dake saman cinyarsa "Na gani......aiki ne me bala'in hatsari da dukkaninmu zamu jefa rayuwarmu cikin hatsari........amma kuma,ranar biyan buqata rai ba'a bakin komai yake ba.......let's try it......idan mukayi winning...." Sai ya saki murmushi yana rufe system din "Zamu kasance mutane mafi sa'ar zuwa duniya" Ya qarasa maganar yana dukan bayan kujerar dake a gabansa. Iya nasarar da yayi musu hasashe ta saka mashkur qyaqyacewa da dariya "Inaso naji dandanonta.....inaso naji ya take.....bansan adadin mafarkin da nayi a kanta,ban taba sanya kwadayina akan wata 'ya mace ba tunda na fara sanin 'ya'ya mata....wannan macen ta zullemin bansan ya take ba sai a kanta,dole ta fahimci wannan kuskuren data aikata!" Ya fada da qwarin gwiwa qwarai da gaske,yana jin ya zaqu da komai ya tabbata. "Bazan iya dogon jira ba Mike.......ka shirya komai tsakanin kwanakin nan biyu" Daga hakan sai kawai ya qarawa motar wuta sosai suna gaggawar ficewa daga layin. *_DUNIYATA LITTAFIN KUDI NE(PAID BOOK),KAI TSAYE KI TUNTUBI WANNAN NUMBER_* 08187255862 50 _Daga ibn juhaim bin haris RA(wannan sunan sahabin annabi ne😄),yace:Manzan Allah S A W yace "da me wucewa ta gaban me sallah yasan abinda yake kansa na sabo,tabbas da ya tsaya(ya jira me sallahn ya gama)tsahon gwargwadon shekara arba'in shine yafi masa alkhairi akan ya wuce ta gabansa_ _Bukhari da muslim ne suka rawaito_ 50 ★Daure da babban towel ta fito daga wanka,qaramin tana tsane doguwar sassalka sumarta dake a jiqe sharkaf da ruwa,alamu dake bada tabbacin wankesa tayi. Idanunta a lullumshe tana jin kalan nauyin da yayi mata saboda kukan da tasha a jiya. Duk da nauyin da zuciyarta tayi mata amma ta wani fannin sai take jinta sawai kamar wani nannauyan dutse dake danne da ita ne ya sauka. Tun daga jiyan data tabbatar ta miqasu hannun da bata haufi akan zasu cutu ko wani abu maras kyau zai samu riskarsu. Tana daga gaban madubin,kadan kadan tana hangen yadda iska take kada labulayen dakin,wata sassanyar iska me dadi kadan kadan tana ratsowa cikin dakin. Lumshe ido ta sakeyi sanda ta gama gyara gashinta ta matseshi cikin ponytail holder bayan ta lanqwasa jelarsa me tsaho sosai,fuskarta ta fito sosai,sai ta sake lumshe manyan idanunta da suka rusuna sosai. Zuciyarta ciwo takeyi idan ta tuna da tuhumar da yayi mata jiyan,tana jin wani zafi cikin qirjinta duk sanda kalmar "Wajen wa kika je?" Ta dawo mata a kunnenta "Me kikayi?" Tana sake sakata jin zuciyarta na matsew a qirjinta. Vibration din da taji daga gefanta shi ya ware zaren tunanin dake qulluwa cikin kanta. Maida dubanta tayi wajen,wayar huda data karba ce wadda ta sakawa charge tun da asuba,bayan wayar ta cika kuma sai ta kunna kanta da kanta kamar yadda tsarin wayar yake. Sunan MAAMAH data gani ya isheta bayanin wacece,wani matsiyacin tsaki taja tana janye idanunta daga kan wayar,sannan ta juya tana wucewa closet dinta don neman kayan da zata saka. Idan ta tuna abinda d'anta da ita sukayi mata,sai taji kanta ya cika da shawarwarin hanyoyin da zata dauki mummunar fansa a kansu kafin ta tattare tabar rayuwarsu. Duk da cewa nashi me sauqi ne,don baiyi yunqurin taba mata kowa nata ba,saidai ya taba mata zuciyarta da munanan kalmomin da koda tayi nesa da rayuwarsa bata jin zata iya mancesu. Har zuwa yanzu da take wannan tunanin ta rasa wanne kalar abu ya kamata ta yiwa maamah?. Abu daya tayi ittifaqi akai shine......tabbas zata banbance mata tsakanin aya da tsakuwa......zata kuma shayar da ita mafi girman mamaki. Tabbas inda tana da ra'ayin d'anta......lallai da zata mallakeshi a gaban idanunta ne,mallakar da babu boka babu malam.......mallaka ta ruwan sanyin da sai ta gwammace bata sanyata a shirmen shirinta ba. Har ta ciro kayan ta dawo ta shirya cikin Palazzo da blouse data kasance cif cif jikinta don bata buqatar kaya masu nauyi kiran bai daina shigowa ba,ta kammala ta feshe jikinta da turare . Scarf ta sanyawa kanta sannan ta taka a hankali tana isa inda wayar take sanda take dab da tsinkewa. Stool taja ta zauna bayan ta daga kiran ta sakashi a handfree ta kuma ajiye saman mirror table din tana tattara hankalinta akai. "Dawa nake magana?" Abinda ya fara fita kenan daga bakin maamah da wani yanayi na zaquwa da son jin wayar a hannun wa take?. Idonta ta lumshe sannan ta bude "Gaggawar ta meye?,kina tunanin wayar huda zata kasance a hannun wani qato ne?,ko a hannun wata sabanin halastacciyar 'yar uwarta data shirya sadaukar da tata rayuwar saboda tasu?". Maganar ta kama zuciyar maamah sosai,ta kuma saukar mata da matsananciyar fargabar data bata tabbacin KOMAI YA QARE saidai a sake sabon zubi da lale. "Naga alamar hakan......kin kuma yi qoqarin sadaukar da rayuwarki ma 'yan uwanki.....ni shaida ce,amma inaso kisan wani abu guda.......kina wasa da baqin kumurcin maciji ne daya shirya dukka dafinsa da xummar harbi ga duk wanda yabi ta hanyarsa" Wani dan murmushi ta sakarwa maamah din tana murza hannuwanta,har yanzu tana jin bata gama dawowa ainihin sabreen dinta ta asali ba......amma kuma da alama komai yana bisa hanyar saituwa "Shi wannan macijin.....idan har yayi sake halittar data fishi sanin kogon da yake kwana yake kuma tunqaho dashi.......tabbas akwai yiwuwar a cimmasa har inda yake......a kuma sanyashi ya yanke wannan kan dake dauke da dafin da kansa da kansa ba tare da yasan hakan ta faru ba....." "Ke dakata qaramar alhaki!" Maamah ta furta bayan dukkan haqurinta ya gaza da yadda yarinyar dake qarqashin igiyar auren d'anta ke iya maida mata magana me zafi haka kanta tsaye......ba shayi ba fargaba,yarinyar da a haife dukka cikin 'ya'yanta ba sa'anta. "Shshshsh....." Sabreen ta fada tana dora yatsanta akan lips tamkar maamah na zaune a gabanta. "Meye na saurin fusata haka?.....ina cewa abun baiyi zafi har haka ba?" Ta furta da alamun murmushi cikin muryarta. "Yaro man kaza......yaro baisan wuta ba sai ya taka..." "Your royal highness......har yanzu bansan meye dalilin wadannan zafafan kiraye kirayen ba da safennan". Iya maqura a rainin hankali maamah tana jin sabreen tayi mata shi,ta dinga qoqarin tausa kanta da daidaita kanta kada yarinyar ta tunzurata furta abinda batayi niyya ba. "Yaro yaro ne.......sabreena......kina da masaniyar cewa nice na tsugunna na haifi fuad?" Dan murmusawa tayi kadan sannan tace "Haka naji labari!" "Amma kina da yaqinin ni na daukoki ko kawoki cikin gidan na maidaki sunan matarsa?.......idan naso qasa da awa biyu rak! Zaki rasa wannan damar?" . Qaramar dariya ta saki ma maamah din,ta gyara zamanta sosai tana kallon kanta a madubi. A yau hirar nishadi take bata a maimakon razani da take samu a kwanakin baya da suka shude. "Kina zaton kina da wani makami da zaki iya fiddani daga gidan yaron naki?........kiyi haquri da abinda zance......amma ko shaidan a yanzu bai isa ya fiddani daga gidan yaron naki da kike tutiya ba........bana son danki ko kadan bazan kuma taba sonshi ba......amma yadda kika sakoni cikin rayuwarku......kika maidani matarsa da qarfin qwanji dana kudi.......to haka fitata daga gidansa da rayuwarku zata kasande bisa zabin kaina a kuma duk sanda nayi niyya......so kibi a hankali,bawai sonshi nake ba.....infact ma baiyimin ba.......amma bazan fita daga rayuwarku ba har sai sanda nayi niyya" "Qarya kike....baki isa ba!" "Dama bance na isa ba......amma zan gwada saiki tayani tabbatarwa...." "Kina kirawa kanki ruwa!,zaki iya rasa rayuwarki ta dalilin haka fa!" "Bari na fara raba naki d'an da rayuwarsa tukunna ki fara ganin kalar wannan baqin cikin kafin ki aiwatar a kaina......zan shayar dashi ruwan guba a ruwan shayinsa na yanzu a maimakon tsubbace tsubbacenki....." Tana kaiwa nan ta kashe kiran tana ma kashe wayar gaba daya. Murmushi ta dinga yiwa kanta a madubi,hirar ta sanya mata nishadi sosai,ko ba komai ta dasa mata tsoro da fargici tabbas na mintunan data ambata. Da gasken haka shine ya faru. Wani irin gumi ya fara tsatstsafowa maamah da wani irin kalar tashin hankali. Zuwa yanzu bata da tabbas akan yarinyar.......tana ji a jikinta zata iya aikata komai da tace din. Kasa zama tayi,jikinta yana rawa ta soma lalubar layin fu'ad tanason gargadarsa akan ya kaucewa komai da zai fito a yanzu daga hannun yarinyar. Kira kusan goma tayi masa a jere saidai ba wanda ya daga,abinda ya sake tsananta tashin hankalinta kenan,ta dinga duban agogo tana qirga mitunan da yarinyar ta kwasa mata. Daidai lokacin ma shi ya jima a office. Ayyukane da yawa a gabansa da suka hade masa saboda jiya bai samu yin komai ba a office din yayi baqi da suka tsaidashi har zuwa dare. Daga jiyan zuwa yau komai zaiyi yana yinsa ne cikin wani irin fushi da zafin ran da hatta saddiq ya fahimci akwai abinda ke damunsa,kuma tabbas ranshi a bace yake. Ture file din gabansa yayi yana jan wani mugun tsaki. A duk sanda ya tuna ko abun ya fado masa a rai sai yaji wani mugun bacin rai yana lullubeshi. Tashi yayi daga kan ainihin kujerarsa yana takawa a nutse,yasa hannunsa yana sassauta tie din dake wuyansa cikin wani irin yanayi da yakejin kamar numfashin da yake shaqa yana masa kadan. "Why i cares so much?" Ya motsa labbansa yana furtawa da wani irin zafi. Ba kasafai yake sanya kulawarsa ko damuwarsa akan komai ba sai abinda yake da muhimmanci a rayuwarsa. Ya tabbatar a karan kansa she's nothing to him amma me yasa abun yake masa zafi "Igiyar aurena" Abinda yake da tabbacin shine dalilin tsaiwar abun a ransa. Sai daya sassauta tie din hade da belt din suspenders din jikinsa,sannan ya jsa ga dispenser dinsa ya tsiyayi ruwan sanyi ya rage sanyinsa ta hanyar zuba ruwan zafi kadan akai,sannan ya koma saman recliner chair din dake gefe wadda aka ajeta don gajeran hutu irin wannan ya zauna akai. Kadan ya samu sassauci sanda yasha ruwan,ya dire cup din idanunsa suna sauka kan wayarsa dake haske. Da farko ya share yana tsammanin fareeda ce data zama kaman wata mahaukaciya. Kusan kullum cikin canza layin da zata kirashi dashi gudun kada yaqi dauka. Layinsa nada wani tsari na hana baqin numbers shigo masa amma nata kiran ya tsallake wannan shingen bai kuma san dalili ba. Sabanin mamakinsa sai yaga maamah. Baya iya qin daga wayarta komai runtsi,duk da daga ita har anni zai wahala su kirashi a irin wannan lokacin,sai ya jawo wayar ya daga yana sanyata a kunnensa. "Kana ina?" Abinda ta fara tambaya kenan tana qoqarin daidaita muryarta "Ina office.....wani abu ya faru?" Ya tambayeta a mamakance "Daga yau wannan yarinyar......." Sai kuma ta dakata saboda wani qaqqarfan gargadi da aka watso mata daga can qasan zuciyarta. Dan jim tayi shima sai yaci gaba da sauraronta baice komai ba "Shikenan,ka kula dai da kyau" Ta yanke tunaninsu su duka biyun da fadin haka. Wani haushi ya cikata bayan ta aje wayar,ita yarinyar zatayi wa wasa da tunani irin wannan?,tabbas idan har ta bari yarinyar ta qara kwanaki uku a gidanma.......bata amsa sunan mariya ba. *_to masu karatu......me maamah zatayi da zai saka auren sabreen qarewa cikin kwanaki uku?.....wanne qwarin gwiwa ko tabbaci sabreen ke dashi wanda yasa taci alwashi ko shaidan bai isa ya kashe mata aure ba?.....muje zuwa jama'a,WANNAN ALQALAMIN NA HUGUMA ZAZZAFA NE_* *_DUNIYATA LITTAFIN KUDI NE(PAID BOOK),KAI TSAYE KI TUNTUBI WANNAN NUMBER_* 08187255862 51 _Daga sumrah dan jundub RA,yace manzon Allah S A W ya kasance yana nemawa mumunai maza da mata gafara a kowacce juma'a_ _harda ni dake da kikazo a wannan zamanin kin shiga ciki,LALLAI HASARA DA TABEWA TA TABBATA GA DUK RUHIN DA BAISON ANNABI,ALLAH KA DAUKI RUYUKANMU RUHINMU YANA CIKE DA MATSANANCIN SONSA S A W_ Sai data fara lalubar number da take da muradin yin magana da ita sannan zuciyarta taci gaba da kwabar data fara mata. "Da kinason gayawa fu'ad me?,ya saki yarinyar?,kada ya amince da ita?,kada yaci abun hannunta?,bayan ke kika aura masa ita?,ke kika bashi tabbaci akan ingancinta da kuma cancantar aurensa da ita?,bayan ko sati biyu ba'ayi ba ke dindai ke kika kafa masa sharadin ya bata kulawarsa?,ya sota?,ya jata a jikinsa?,kinason dabawa kanki wuqa?,kinason sanya wani zargin saman zargin dake kansa naki?". Wannan tunanin ya sakata sakin ajiyar zuciyar tana kiran number da tazo kai,a gefe guda tana mamakin abinda ya hana hajja nemanta ko zuwa gurinta ko tuntubarta akan matsalar da ta shaida mata jiya,TABBACIN DUKKAMIN MAGANGANUN LAILA BA QARYA KO SHAKKA AKAI KENAN. Sai taja qwafa tana gyada kai "Duk wanda yaci tuwo dani miya yasha" Ta furta a bayyane,daidai sanda taji an murda qofar dakin an shigo laila ta bayyana. Da kallo tabi lailan har zuwa sanda ta qaraso gabanta. Ta durqusa saman gwiwoyinta wani abu da bata taba yiwa maamah shi ba duk da matsayinta na qawar mahaifiyarta shekara da shekaru. "Ina kwana maamah" Ta furta cikin tsantsar ladabi har bata iya hada idanunta da nata. Kai ta daga ta kalleta,dukka wani bayanin plan nasu da lailan tayi mata jiya sai ya shiga dawo mata kanta tar tamkar a lokacin take labarta mata. Wani bacin rai da radadin da wanda akaci amana keji ya taso mata,sai ta maida kanta ga waya kawai tana tura masa saqo. Sai data tabbatar saqon ya shiga sannan ta kalli laila,wadda kafin lokacin duk wani kalar tashin hankali laila ta shigeshi. Tana jin kamar ta dora hannunta aka ta yita zunduma ihu,iya yadda maamah taqi amsa mata gaisuwa ya sanyata cikin firgicin kodai wani laifi tayi mata?. A yanzu a rayuwa bata jin akwai wani abu da zai daga mata hankali sama da taga fushin maamah.....ko kuma tayi wani abu da zai saba umarninta. "Lafiya qalau....." Amsa matan kawai da tayi ya sanyata sakin wata sassanyar ajiyar zuciya,tana godewa Allah da ba wani abu tayi daya bata mata rai ba. "Na shiga dakinki naga basu shareba.....na gyara miki,saiki duba idan akwai abinda baiyi ba ki gayan a sake gyara mikin". A nutse take qarewa laila kallo,ji take a ranta inama ace fu'ad ne haka a gabanta yake wannan bayanin bawai laila ba?,inama ace aikinta ya fada daidai?,i yanzu da batasan wanne irin farinciki take ciki ba.....lallai da zata kasance wata halitta mafi farinciki a fadin duniya,ta qarasa wannan tunanin tana runtse idanunta gami da budesu. "Basai na duba ba,saidai anjima kafin na kwanta ki sake" "To ba matsala.....waida so nake naje wajen hajja.....jiya muna magana bamu gama ba kika kirani" Kai ta girgiza,duk da tanason sake samun information,don tayi imanin duk abinda zasu tattauna tamkar a gabanta za'a yishi,to amma kuma tana buqatar ta kammala da aikin sabreen tukunna......tabbas komai da zai biyo baya me sauqi ne. "Ki kirata ki gaya mata nace ba yau ba,zan duba gobe na gani idan ya dace kije goben" Ta fada kanta tsaye tana ci gaba da riqon wayarta cikin jiran tsammanin shigowar kiran hanzari nan da kowanne lokaci. Sanda laila ke gayawa hajja saqon maamah kai tsaye murmushi ta saki bayan sun gama wayar tana jinjina kai "Mariya!.....Mariya,zan miki babban karatun da gogewarsa sai a cikin kabarinki,a sanda qasusuwan mowacce halitta ta jikinki ta gauraye da qasa,kin bani qofofi masu yawan gaske ba tare da kin sani ba.....zan shiga ta kowacce qofa......na fita ta kowacce qofa.....na shiga kuma cikin rigarki na dimauta duniyarki......sannan na hana muradinki da mafarkinki su zama gaskiya" Abinda ta fada kenan tana qurawa wayarta idanu dake aje tana ta burarin nemon taimakon a daga kiran daya shigo. Tun safen har azahar zuwa la'asar da tayi dukka cikin dakon shigowar kiransa take. Sai bayan la'asar din liqis cikin ba zata daya daga cikin masu aikinta suka shaida mata tana da baqo me suna hanzari. "Ki rakoshi can cikin setting room,kada a barshi a waje" Ta fada cikin doki da zumudi,ta miqe tana daukan dankwalinta ta maida kanta,har ranta tana jin mafita tana tunkaro ta. Fitowarta ya sanya hanzari sauke qafafunsa da suke dore daya saman daya. Sanye cikin baqar shiga,wandon jeans da shirt dukka baqaqe,sai baqar hular Ascot cap daya jawota tadan rufe fuskarsa kadan. "Barka da fitowa" Yayi maganar yana miqa mata nannadaddun takardun dake hannunsa,sai ta fasa zama ta sanya hannu ta karba sannan ta zauna dasu ta soma budewa tana cewa "Aiki dakai akwai jan kudi.....amma kuma akwai hanzari kamar yadda sunanka yake" Ta fadi a nutse tana bin list na sunayen da kallo da kuma hotunan. Sai data gama qare musu kallo tas sannan ta kaudasu daga fuskarta tana kallonsa "Kin gansu hajjaju?" Ya rigata fada,sai ta gyada kai ranta yana yin fari. "Kayi qoqari sosai hanzari.....amma waye kake ganin ya dace mu dauka?" Ta fadi maganar tana sake kallon list din. Matsowa gaba yayi kadan ya miqa mata hannunsa yana cewa "Kawo nan ki gani" Ba musu ta miqa masa,ya aza takardar saman teburin dake tsakaninsu yana binsu da yatsa daya bayan daya,kafin daga bisani hannunsa ya tsaya daidai fuskar mashkur,sai ya daga kai yana kallonta. Duk da baiyi magana ba bai kuma ce komai ba amma maamah ta fuskanci abinda yasa gaba da abinda yake nufi. Sai ta zuba masa idanu tana sauraron qarin bayaninsa. "Wannan shine mashkur......dan tsuntsu me wayo kenan..." Yayi maganar yana sake xuba yatsunsa saman fuskar mashkur. Sake jan hoton gabanta tayi,tunda ya aje din dama kusan fuskarsa tafi jan hankalinta. Yana da kyau daidai misali,wanda zaiyi daidai da plan dinsu,ta jinjina kai tana duban hanzari "Yayi......a tsara komai.....amma karka manta,secretly" Ta fada tana nuna hanzari da yatsa. "An gama" Ya furta yana murmushi. *FAREEDA* Ci gaba tayi da duba bayanan,murmushi yana sake wanzuwa saman fuskarta. Murmushin da takejin yana gauraya da farinciki da take da yaqinin zai zame mata tabbatacce ta hanyar samarwa da zuciya da ruhi abinda sukesu ta sassauqar hanya. Sake bude shafin qarshe na takardun tayi,take hotonta ya mamaye screen din tab din nata gaba daya,shafin qarshen daya zama shine na qarshe data bude cikin dukka bayanan data samu. Ta barshi a qarshe ne saboda dukka sauran shafukan na dauke da full details da bayanan da suka faranta mata rai sosai,sukayi kuma daidai da muradinta. Hoton sabreen din daya cika allon tab din ta zubawa idanu. Wani abu yana tsarga mata tun daga tsakiyar kanta har zuwa tafukan qafafunta. Wani mahaukacin wutar kishi ke ruruwa cikin zuciyarta. Ta kusa kwashe sakanni talatin a haka,kafin ta dafe dukka hannuwanta saman kujerar da take kai tayi zullo zuwa gaba har a sannan ta gaza dauke idanun nata. Labbanta suka motsa kadan rana son kiran ainihin sunan nata,saidai ya tsaya ne can qasan maqoshinta ba tare da sautin harafin ya fita ba. Adan hanzarce ta maida hannunta saman tab din tana komawa shafin da yake da alaqa da komai daya shafi sabreen din,ta sake karantawa sosai kamar me shirin haddace komai daya shafeta "How comes?" Ta tambayi kanta tana yamutse fuska lokacin da takai qarshen bayanan "Karuwa?......How did he get married to her?" Ta sake tambayar kanta da kanta "She's karuwa officially fa?" Ta kuma nanatawa cikin zallar mamaki. Ba wata amsa data samu daga kowanne sashe na kwanyarta,saita dage kafadunta duka biyun sama tana sakin murmushi,lallai komai zai tafi da alama daidai "Fu'ad isn't your type madam.....its over between you too" Tayi maganar tana nuna hoton sabreen da dan yatsa,saidai ba abinda ya canza zuciyarta daga mahaukacin kishinta da takeji. Ta kowacce fuska,ta kowanne bangare sabreen din ta yaga mata indai ana batun kyau ne da sassanyan zubi da ta tabbatar yana daya daga cikin abinda ya fusgi hankalin fu'ad din,banda hakan.....yadda ta samu full details dinsa zai wahala ya nuna interest akan karuwa har ya aureta. "It's my turn......my time to shine has come" Ta fada da qwarin gwiwa,ta miqe tana nufar closet dinta ta sauke luxury luggage dinta guda daya ta fara selecting kaya tana shiryawa a ciki ba tare da jiran kowa cikin masu aikinta ba. Cikin qasa da mituna sha biyar ta gama packing komai da komai nata,sannan ta dawo ta dauki wayarta ta kira number abbanta. "Hello dad....." Ta fada a shagwabe. Ita din 'yar gaban goshinsa ce da dukka yaransa babu wanda ya kamo matsayinta a zuciyarsa. A kullum tana maida kanta tamkar 'yar shekara goma a gabansa,haka shima yake biye mata,saidai hatsabibancinta da girman izzarta ta dara tashi shi da yake da muqamin ambassador din gaba daya. "Dad.....ayimin booking flight please......gobe nakeso if possible,it's an urgent dad..." Ta furta a shagwabe kamar yarinyar dake tsakanin shekara shida zuwa bakwai "Thank you dad" Ta fada da murnarta jin ya bata tabbacin zaisa a mata booking private jet. Da murmushi sosai a fuskarta ta soma turawa zababbun qawayenta da za'ayi tafiyar tare dasu request. Cikin qasa da minti goma ta gama komai,sai ta sauke wayar ta matsa gaban dan wani madaidaicin table dake dauke da tukunyar shi sha ta fara qoqarin hadata. Tanajin a yanayin da take ciki na farinciki ita daya zata tayata sarrafa murnarta, Kyakkyawar zuqa tayi mata tana bulbular da iskar daga dukka qofofin hanci da bakinta,ta lumshe idonta fuskar sabreen na mata shawagi tsakanin tunaninta da qwayar idanunta "Blast it!" Ta fada da qunan zuciya tana kaiwa iska naushi,tana jin kaman tayi using acid ta dauke wannan kyan da ya hanawa zuciyarta sukuni. *_DUNIYATA LITTAFIN KUDI NE(PAID BOOK),KAI TSAYE KI TUNTUBI WANNAN NUMBER_* 08187255862 52 _Daga dariq dan shihab RA,manzon Allah S A W yace "juma'a haqqi ce kuma wajibi akan kowanne musulmi yayita cikin jam'i,sai akan mutum hudu kawai(ta sauka),MACE,BAWA,YARO DA MARA LAFIYA"_ _Abu dawud ne ya rawaito_ ★Shuru ne ya biyo baya duk da wayar tana riqe a kunnenta. Dukka bayanan zuwaira ta gama saurara wadanda suka gama bata tabbacin lallai da gaske yaran sunyi nisan da ba wanda zaice ga inda suke......uwa uba kuma yarinyar tana ci gaba da harkokin gabanta hankali kwance kamar ba wani qalubale a gabanta. "Ni kaina yanzu komai na taba ko nace zanyi mata dakatar dani takeyi,waccar munafukar me aikin da ameena ta kawo mata yanzu da ita takeyi,munafuka me shegen iyayi da bariki,idan kikaga yadda takeyi mata zaki rantse da Allah sabreena ce babba ba ita ba". Wani tattauran yawu maamah ta hadiye,tsananin bacin rai yana sake cikata "Ki saurara,ki sanya dukka kunnuwanki da hankalinki dama idanunki kan gidan......kada kice komai,kuma kada kiyi komai,akwai gagarumin al'amari da zai faru cikin gidan.....abu daya nakeso kiyimin,ki kasance me bibiyar diddiqi bayan faruwar lamarin" Abinda maamah ta gaya mata kenam ta kuma yanke kiran. Bin wayar tayi da kallo......har a sannan tanaji a ranta muddin tabar sabreen din taci galabar ci gaba da rayuwa tana shan inuwa da arziqin danta lalallai ba shakka bata cika mariya. Shekaru da gwagwarmar rayuwa da gogayya da tayi da kalar mata daban daban bai amfaneta da komai ba.....shekarun data kwashe ma a duniya basuyi mata amfanin komai ba,dole ta fiddota daga gidan......wannan shine zai bata damar yin walagigi da rayuwarta da kuma d'aid'aita rayuwarta kamar yadda ta d'ai d'aita mata burinta. Qarfe daya da rabi na rana driver din hajja ya faka motarsu qarqashin muhallin da aka tanada saboda ajiyar motoci. Koda ya tsaida motar ya kuma kasheta amma hakan bai sanya hajja fitowa daga cikin motar ba. Da idanu take bin kowanne sashe na ginin gidan da kallo tamkar yanzu ta fara ganinsa. Saidai sam a badini ba wannan bane damuwarta ba......ba kuma shi take kallo ba. Tana nazarin yadda ALKHAIRI ya juye izuwa SHARRI,ta gama tura mota tsaf tana shirin buleta da balbalin hayaqi maras dadin shaqa?,hayaqi mafi cutarwa cikin qofofin hanci da kwanyarta?.. Wata gauruwar ajiyar zuciya ta sauke,sannan ta balle murfin motar yau da kanta tana fitowa,sabanin a baya da sai driver ya fito da kansa ya bude mata sannan ta fito. Gyara yafen mayafinta tayi,kanta tsaye kuma take takawa zuwa hanyar da zata sadar da ita da ainihin cikin gidan. Duk taku daya idan tayi la'anar maamah take cikin ranta,tana ji a jiki ta jefeta a wata kalar musiba da batasan ranar fitarsu ba. Zuciyarta tana mata wani qunci da ita kanta batasan iya adadinsa ba......amma wani sashen na zuciyartata yana sake jaddada mata "Fushi ba naki bane.....nasara bata masu gaggawa ko saurin fushi bace!" Wannan shine abinda yaketa mata burki take hadiyewa da qyar. A jiya da qyar bacci barawo ya dauketa,cikin fargaba da tsoron fitar dukkanin sirrinsu daga bakin laila..... Yanayin aikin bokansu dabanne,a aikin da aka tanadarwa fu'ad harda na rariyar baki,wanda baida wani sirri na kansa sai abinda maamah ta buqaci ya sirranta,muddin maganin yayi tasiri a jikin laila kamar yadda aka tsara.....hakan yana nufin duk wani sirri nata yanzu a tafin hannun mariya yake?. Wannan tunanin ya hana mata cikakken bacci da safe,ta dinga qididdiga da lissafin wucewar sa'o'i don ta samu ta fito zuwa gidan mariyan. Tanaso taga yanayin fuskarta,abinda zai nuna shine zai zame mata amsa na abinda take zato da zargi. Duk da cewa na tsuburi ya mata alqawarin ba abinda laila zata iya gayawa maamah.....to amma tasan aikin bokansu daban yake dana kowanne boka. Sau daya tak! Yake maka aiki.....idan har yayi maka na biyu to tabbas ka taki sa'a,uwa uba yawan yawan ayyukansa basu da makari.....shi yasa ta jima tana murza zaren rayuwarta ta kowanne fanni.....a yanzu kuma bata fatan wata matsala tazo mata ta wannan fuskar. Idanunta akan parlor din maamah.....falon da kullum maamah din ke kusheshi da ganin tsadar kayan adon ciki bai kama qafar na gidan alhaji hamza ba.....Parlor din da ita kuma hajja harira kullum kwanan duniya ta daga kai ta kalleshi sai kishin zamowarsa mallakar mariya ya baibaye zuciyarta da wata irin hassada me tsananin qarfi. Iya bariki da qwarewa wajen boyewa koma waye yanayin da kake ciki ya sanya maamah din bata taba fahimtar komai ba. Takun da taji ana fitowa daga kitchen ya sanyata waiwayawa cikin tsammanin daya daga cikin masu aikin gidanne wadanda su zasu yiwa maamah maganar ta iso tana son ganawa da ita. Amma kuma sabanin hakan,laila ta gani a gaba,dauke da kwando cike da warmers kala kala,saman rigar jikinta kuma apron ce a daure. "Laila?!" Ta kira sunanta cikin qaraji da wani kalar madaukakin mamaki tana takawa da hanzari don isa gabanta. "Sannu da zuwa hajja" Lailan ta furta fuskarta shimfide da murmushi dake nuna ba wani abu da takejin ba daidai bane "Bari na ajewa maamah abincinta nazo mu gaisa" Ta furta tana wucewa dining din. A nutse ta shirya komai.....kamar ba lailanta diyar gata ba,lailan da idan taci abinci ko kwanon da taci abincin batasan ta janyeshi ba......lailan da saidai tana mimmiqe saman sofa ko gado ta zabi abinda take da sha'awar ci.....wannan lailan itace yau a kitchen da rigar 'yan aiki?. Sanda ta kammala shiryawar saita dago tana murmushi,suka hada idanu da hajjan tace "Ina wuni?,na kira miki maamah din?,Allah yasa bata kwanta bacci ba don tace ko waye yazo kada a tasheta" "Gani nan laila baccin baizo ba....kun gama ne?" Maamah dake saukowa daga stairs din ta fada. Tare suka daga kai suna dubanta,sanye take da applique lace purple color da ya dan ciza kadan,dinkin doguwar riga da aka qawatata da wani irin dinki me daukan hankali. Shigar tabi jikinta....wadda ke bayyanar da zallar izzarta da isarta. "Kun gama laila?" Kai ta shiga gyadawa kaman mara hankali da sauri "Mun gama maamah ko akwai wani abun?". Ta fada a rusune. Murmushi maamah ta saki tana dafa kafadarta "Amma dai yau kin koyi yadda ake dambun gargajiya da kuma liver salad ko?". Murmushi ta saki kaman wata shashasha "Sosai ma maamah.....ai kin taimaken na gode sosai". Ta fada tana rusunawa a wajen. "Shikenan,yanzun zaki iya yin wanka,idan kin gama kiyi zamanki a daki kada ka fito yanzu" "To maamah" Ta amsa mata a ladabce tana juyawa ba tare data dubi ko bangaren da hajja take tsaye ba. Idanu suka hada da hajjan,wata tayi wata irin mutuwar tsaye. Gefe guda kuma taci gaba daya tamkar qwaqwalwarta ta daina aiki ne gaba daya. Wani qaramin shu'umin murmushi maamah ta saki,ta juya da hanzari bangare da laila ke tafiya "Au.....nikam nace kin gaida mamanki kuwa?" Kai ta girgiza tana fadin "Bakice ba ai". Fuska kadan maamah ta bata "Haba ke kuwa auta.....yarinyar kirki,zo ku gaisa mana....wataqila sanda zata tafi ai baki fito ba". Dawowa tayi ta rusuna har qasa tana gaida hajjan abinda bai taba faruwa ba kenan tsahon rayuwarta. Da fari idanuwa kawai hajjan ta saki tana kallon lailan,har sai da taji lailan ta maimaita gaisuwar sannan ta duqa tana dagota daga tsugunnon da tayi "Ki dauko mayafinki kizo mu tafi gida" Ta fada muryarta na rawa amma tana qoqarin danne rauninta don bata fatan maamah din ta gani. Kai ta girgiza tana duban maamah wadda tayi kaman batasan abinda ke faruwa ba,tana laluben wajen zama hankalinta akan fuskar wayarta "Nafison nan hajja.....ni ki barni a nan" Ta fada tana zamewa daga jikin maamah din ta wuce abinta hankalinta kwance zuwa hanyar dakin da aka bata. "Bismillah.......zauna mana surukata" Maamah ta fada fuskarta a sake. Kalmar suruka din da maamah ta fadi shine ya sanya hajja jin wani abu tamkar wutar lantarki ta fusgeta. Cikin qasa da minti guda gumi ya fara tsatsatsafo mata ta kowacce kafar gashi ta jikinta. "Atika!" Maamah ta qwalawa me aikinta kira,wanda cikin qasa da minti daya ta bayyana,sanin da sukayi mata batason ta kiraka ka samu jinkirin zuwa. "Dauki remote ki kunnawa surukata A.c,karki saka da yawa kada kuma ta saukar mata da zazzabi" "To hajiya" Atika ta fada da rawar jiki tana me aiwatar da abinda maamah ta umarceta. Zagayawa kawai kalmar takeyi cikin kunnuwan hajja.....indai har kalmar surukuta zata fita daga bakin maamah a wannan yanayin,lallai ne ba abinda bata sani ba kenan. "Ki maida hankalinki jikinki hajja......har mariya ce zata firgitaki har haka?". Wani sashe na zuciyarta ya bata qwarin gwiwa har ta samu qarfin halin tattara 'yar nutsuwar jikinta tana neman wajen zama gami da fuskantar maamah. "Mariya......zuwa nayi na duba lafiyar laila.....ya kuka tashi?". Murmushin nan dai ta kuma saki,sannan ta ajiye wayarta a gefe tana bada hankalinta gaba daya a kan hajja "Laila tana lafiya......kuma zata ci gaba da kasancewa lafiya sumul a hannuna......kinsan na iya riqon 'ya'yan jama'a" Ta fada hankalinta kwance. Murmushin qarfin hali hajja ta saki,sannan ta jinjina kai "Ai na sani mariya......mun tashi lafiya?" "Lafiyarmu sumul qalau hajja....." Daga nan ta fada nazarin da wacce kalma zata tunkareta. Idanunta ta daga tana duban maamah. "Muna magana jiya sai kuma Kira ya yanke....." "Eh wannan case din na gama solving nasa,saura fitar result" "Zancanmu fa kan laila da fu'ad?" Hajja ta jefa mata tambayar kai tsaye,duk kuwa da cewa ita kanta me bawa wani amsa ce.....saidai tanaso takai mariya inda take buqatar aje. Buda baki maamah tayi da nufin cewa wani abu......amma sallamar jarma daya daga cikin masu gadin gidan yayi sallama daga can bakin qofar falon. "Malam jarma ya akayi?" Maamah ta buqata sani sanda yake duqewa a wajen "Baqi gareki hajiya......ban sani ba zasu iya qarasowa ko a maidasu?". Fuskarta da dan mamaki take dubansa "Baqi kuma?,daga ina?" "Diyar ambassador Khaled mustapha ce,haka tace a gaya miki". Wani madaukakin mamaki ya cika maamah din,ba ita kadai ba,hatta da hajja sunan yaja hankalinta qwarai da gaske. Miqewa maamah din tayi tsaye tana dubansa "Maza ayi mata izini ta shigo......na tabbatar koma meye ya kawota nan,silar haihuwar ALKHAIRI ne fu'ad" Ta furta tana jin wani irin alfahari da haihuwarsa fiye da kowanne lokaci. Uwa uba tana yine da biyu,don ta tabbatar gaba daya hankalin hajja yana kan abinda yake faruwa. Sanye take da wani matsiyacin yadi da aka narkar da kudade masu nauyi kafin siyansa da yagalgalashi,aka kuma yi masa dinkin fitted gown data zauna a jikin laila......kai kace a jikinta aka dinkashi. Yadda dinkin ya zauna mata a jikinta.....hatta da dagawar numfashi daga cikinta da qirjinta kana ganin gudanarsa. Ba mayafi a jikinta,sai dankwalin material din da aka mata wani dauri dashi saika rantse hula ce ta kafata. Wasu nau'ikan dan kunne manya ne a kunnenta,wanda suke tafe da.manyan banguls da suka dace sak kalar material din jikinta kamar a company daya aka qerasu. Highhill ta sanya masu tsananin tsini sarqafe da igiyoyi,kaman yadda qwayar idanunta ke saye da tafkeken glass daya kusa cinye rabin fuskarta. Labbanta kwance reras da lip gloss,iya wannan kadai zai gaya maka tafiya akayi irin ta masu abun,ba wahalar hanya tunda sararin samaniya ne yayi aikin. Yadda take taku daya bayan daya tana takowa ciki,idanunta kan kowanne sashe na parlor din tana yaba alatun da aka zuba.....haka bakinta ke bada satin qas qas na chewing gum din da take taunawa cikin bakinta. Tana daga tsakiya,gefe da gefanta kuma fitattu kuma manyan qawayenta ne,lubna da jalilah,daga bayanta kuma masu aikinta ne data taho dasu suma guda biyun. Fuskar fareeda ba boyayyar fuska bace musamman idan kaidin ma'abocin kallon news ko dabdala a social media ne. Kusan duk wani motsi na mahaifinta ko na siyasarsa zaka ganta a ciki zaka kuma tsinceta a ciki dumu dumu. Lafiyayyen murmushi ya kubcewa maamah,ta taka a hankali tana marabtarsu. Doso sun da maamah tayi shi ya sanya laila cire glass din fuskarta dukka a qoqarin ta na nunawa girmamawa ga maamah din. Cikin qasa da minti biyar suka yiwa kansu mazauni a parlor din,sannan kuma gabansu ya cika da nau'in kayan ciye ciye daban daban na alfarma. "Nasan zakiyi mamakin zuwana wajenki maamah?" Ta fada tana qoqarin karyar da muryarta. Kai maamah ta jinjina,tako ta ina tanajin wani girma yana hawa kanta 53 _Daga abu hurairah Allah ya qara yarda dashi yace:mazan Allah S A W ya ambaci ranar juma'a,yana cewa "A CIKINTA KAWAI WANI LOKACI,BA WANI BAWA MUSULMI DA ZAI RUSKETA YANA ME TSAIWA YANA SALLAH YANA ROQON ALLAH WANI ABU FACE SAI ALLAH YA BASHI ABINDA YA ROQA DIN". sai manzon Allah yayi nuni da hannunsa na qanqantar lokacin (ma'ana baida tsaho,Allah yasa muna cikin wadanda zamu yita ruskarshi)_ "Eh to.....zai iya kasancewa abun mamakin ta wani fuskar,ta wata fuskar kuma ba abun mamaki bane,musamman idan kikayi duba da irin kalar zuri'ar da Allah ya bani" Tayi maganar da nufin jifa ga ma'anoni guda biyu tana gyara zamanta. Kai laila ta jinjina tana tsare maamah da ido,tun kafin tazo ta hadu da ita tasan wacece ita,don haka ko sau daya bataji d'ar ba na samun nasara ta hannunta ba. "Ko zamu iya kebewa muyi magana?" Laila ta fada tana duban maamah. "Me zai hana?,bismillah" Maamah ta fada tana miqewa,sannan ta fara takawa,sai kuma ta tsaya tana duban hajja,wadda keta kokawa da zuciyarta akan tayi abinda ya kamata "Yi haquri hajja.....zamu gana,yanzu zamu fito" Ta fadi mata tana sakin wani murmushi dake dauke da ma'anoni da dama. Sabon mariya ne......jifan maqiyi da murmushi ko kuma abokin adawa,wannan shine kusan makami na farko da take fara yaqar zuciyar abokin burminta,yayi tsammanin ita din wawiya ce.....itadin ba wani abu da zata iya,saidai kuma daga qarshe reshe ne yake juyewa da mujiya,sai taje maka da wani irin kalar farmakin da zaya kaika qasa koda baka shirya hakan ba. Bata da cikin mutanen da mariyan zata iya farmaka ta haka har kuma ta samu galaba,saboda sanayya ce ta kar da kar,ba wani abu ko hali nata da zata layance mata dashi. Dan madaidaicin parlor din shima sai daya ja hankalin laila,duk da ba wani baqon abu a ciki wanda bata sani ba.....amma yanayin tsarin da yadda aka zuba komai luxury ya bala'in shiga ranta. Wannan karon maamah ta fahimci haka,saita jefeta da murmushi sanda take zama tace "Hala kema ya burgeki?,aikin muhammaduna kenan.....komai nasa me tsari ne". Lumshe idanu laila tayi tana sake ji yana kuma shiga ranta,jini da jijiya harma da b'argonta qaunarsa tana sake ratsata "Inama zaki lamuncemin na zama matarsa.......bisa farashin dala dubu d'ari" Ta furta qasa qasa tana kallon maamah. Zubawa laila idanu tayi sosai tana jin sautin muryarta yana zagaya dakin,duk kuwa da cewa ta kammala taqaitaccen bayanin nata dake qunshe da saqo me tsananin nauyi.....ci gaba tayi da kallon laila tana son tantance Gaskiyar abinda ta fada ko kuma akasin hakan.....magana ake ta kusan million dari da hamsin ko da sittin fa......kawai don tanason fu'ad?,kawai don tanason ta aureshi?. Wane sashe na zuciyarta da kwanyarta da yake da kaso mafi girma wajen tsara mata komai ya harba,wannan ya sanya duk wani abu data shirya ambatawa ya wargaje,take ta sauya yanayin fuskarta daga me yalwar fara'a zuwa tsukakkiya "Wane irin magana ne wannan?,ance miki neman kai nakeyi da yaro na?" Tayi maganar a dake cikin qoqarin nuna bacin rai,da kuma tankwabar da tayin gwaggwabar garabasa da ribar da zata iya samu. Ga mamakinta murmushi laila ta saki,hankalinta kuma a kwance ta koma tayi relaxing jikin kujerar tana duban maamah,sannan a nutse ta daga qafarta ta dora daya saman daya tana ci gaba da dubanta. "Karki wahalar da kanki.....kada kuma ki wahalar da shari'a,kada kiyi kaman bakison kudi hajjiya......idan sun miki kadan kawai kice na qara miki,sai na qara mikin a wuce gurin.....fu'ad kawai nakeso,kudi ba matsalata bace sam sam". Sake tsare laila tayi da ido a karo na biyu tana karantar gaskiyar abinda take fada har zuciyarta. Qwaqwalwarta ta lula zuwa duniyar tunani duk da bata barta tayi nisan zango ba. Akan me zata bari tayi asarar kudin da take gani a gabanta yanxu haka?,bayan tana da damar mallakarsu?. Tabbas akawai manufar turo laila da ubangiji yayi cikisu a daidai wannan lokacin da take neman dukka hanyar da zata cisge sabreen daga gidan fu'ad.....babu ko shakka laila itace macen daya dace ta maye mata gurbinta. Duka ma a ture ta batun kudaden da zata mallaka......babban abun alfahari ne a yadda ubangiji ya yiwa yaronta kudi yabi sahun manyan masu kudin africa ma gaba daya......ace kuma yau shine yake auren diyar mutum kaman ambassador khaleed mustapha,wanda a muqamai dai na duniya tana jin ba wanda bai riqe ba,saidai kuma a lahira idan ana riqewa. Lallai ne ita mariya sunanta yana dab da sake fantsama cikin bakunan al'umma.....qawaye dangi da 'yan uwa,tana dab da sake taka wani matsayi na zama cikin manyan matan da fu'ad har yanzu yaqi sakar mata jelar macijin tayi wasa da ita da kyau,....wannan shine mafarin da tauraruwarta ta gaza yin haske kaman yadda takeso. Sunanta takeso ya zama cikin jerin sahun sunayen mata masu aji da sukafi kowanne mata a africa da duniya ma wasa da kudi.....cikin jerin sunayen iyayen attajiran 'ya'ya da kowanne taro ake kwadayi da rububin gayyatarsu,saboda sun zama bangon sugar ko na zuma,masu yayyafin kudi in dollars not in naira......don tana jin zuwa yanzu a arxiqinsa ita kanta tafi qarfin yin kyauta da naira. "Ki rubuta dukka adadin da kikeso" Ta tsinci muryar laila tana fadi,saita sauke idanunta akan abun rubutun da laila ta aje a tsakaninsu tana rutsata da idanu. Maida dubanta tayi kan fuskar laila,duk da alamu sun nuna tasan wani abu a kanta......amma ba zatayi saurin bada kai bori yahau ba haka da wuri gudun raini. "Ba ta wannan nake ba.....kawai ina duba cewa mahaifinki babban mutum ne da yakai kowacce uwa taso hada jini dashi.....ko don saboda shi zan shige miki gaba har ki samu fu'ad.......amma samun muhammad ba abu bane me sauqi......da gareshi akwai wasu tsauraran matakai,kamar yadda nima daga wajena akwai wani mixani da nakeso duk matar da zai aura lallai saita cikemin su cif da cif......yanzu haka rashin cike wancan mizanin daga matarsa ta yanzu ya sanya take fuskantar barazanar gutsirewar aurenta daga yanxu zuwa kowanne lokaci" "Daga yanzu zuwa kowanne lokaci?,ashe ma baki da guarantee......ashe baki da tabbas?" Laila ta fada da narkakkun idanunta dake nuna yadda suke da kyakkyawar alaqa da kayan maye "Ai kawai kiban wannan kwangilar.......nan da jibi ko gata.....kwanaki uku idan sunyi yawa zata zama tarihi a rayuwarsa......shiga cikin mutane xai gagareta......bama ita kadsi ba,haka dukka wani dake da nasaba ko alaqa da ita" Tayi maganar da cikakken qwarin gwiwar daya sanya maamah tsayawa ta xubawa laila ido. Daga jin alwashin dake fita daga bakin laila kadai ya isa ya gaya maka ita dinma wata akwai wani magana ta daban a kanta......itadin ma a shirye take "Dole kema nayi takatsantsan dake.....aminta dake haka lokaci guda babban kuskure ne......amma dole na fara miki da karin maganar nan da hausawa ke fadin DUK WANDA YA RIGAKA KWANA DOLE YA RIGAKA TASHI. Murmushi ta sake mata tana dubanta,ta sake yalwata fara'ar dake saman fuskarta tana kallonta. "Wannan ba wani abu bane da zai zama matsala......na baki wuqa da nama.....idan akwai wani information da kike buqata dukka a shirye nake na baki shi". Kai laila ta jinjina tana sakin murmushi " Zan iya gaya miki har fiye da abinda kika sani......ina da labarin abinda na tabbatar ke baki sanshi ba". Ta qarashe maganar tana bude handbag dinta qirar kamfanin Hermes ta zaro cheque. Rubutu tayi samansa hankali kwance tayi kuma sign dinta,sannan ta miqawa maamah. Kudi ne a rubuce kamar yadda ta furta zata bayar da farko,maamah din bata gama wannan tunanin ba muryarta ta sake fargar da ita "Wannan din somin tabi ne.....muddin kikayi nasarar zama surukata,zaki mallaki wata power ta fada a ji a manyan gurare da dama ta hannun mahaifina". Komai ganinsa maaamah ta dinga yi kaman cikin mafarki,duk da ta tattara dukka mamakinta ta hadiye don ba buqatar laila ta karanci komai. "Zamu iya ganawa dashi a yau?" Laila ta tambaya maamah tana jin kwadayin ganinsa a daren yau. "Baki da matsala da wannan" "Zamu wuce masauki yanzu haka don mu huta sosai,bayan magrib sai na dawo,hakan yayi?" "Yayi" Maamah ta fada tana daga zaune har yanzu,don mamakin da taketa boyewa yaqi barin zuciyarta. A gabanta Laila ta miqe tana fita daga parlor din,maamah kuma ta rakata da idanu. Tana fita daman jira takeyi,ta miqa hannu ta jawo cheque din tana dubawa "Da gaske adadin ta rubuta,akwai genuine din signature nata da komai?" Sake jujjuyashi tayi a hannunta,sai kuma wani murmushi ya qwace mata. "Lallai ni mariye me sa'a ce,ko rashin samun fu'ad a hannu akan lokaci na yarda lokaci kawai ne baiyi ba" Ta gayawa kanta da kanta tana gyara zamanta sosai tana jin kamar kanta zai fashe saboda wata izza da take saukar mata har tsakiyar ruhinta. Ta zubawa guri daya idanu murmushi na fita daga fuskarta lokaci bayan lokaci. Yau da wacce irin sa'a ta tashi?,wacce addu'a tayi yau?,babu....shine amsar data bawa kanta da kanta,don ko basmala cikakkiya bata jin tayi tun daga safe kawo yanzu. A dan fusace ta juyo jin an murda qofar ana shigowa,saboda ita din bata sakarwa kowa da kowa shigo mata guri kai tsaye ba....ko waye kai saika nema izini ta kuma baka. Idanu suka zubawa juna ita da hajja,saita janye cheque dinta tana lanqwasheshi ta daga pillow din kujerar gefanta ta saka a qasansa. Idanun hajja yana kai,abun kuma ya sake haifar mata da wani matsanancin bacin rai. Iya wannan abun da mariya takeyi kawai ya isa gaya mata komai daya faru ya faru ne bisa son ranta da kuma zabinta. Tunda suke da mariyan ba rufa rufa irin wannan tsakaninsu......tayi baqi ta kasa ganawa dasu a gabanta?,taga takarda duk da batasan ta mece ba amma mariyan ta jata ta boye?. "Kinga surukarki ko?,diyar ambassador khaleed mustapha" . Maamah ta sake maimaita abinda tasan already hajjan ta jishi. "Musaddiq ne kenan shima????". Kai da maamah kr girgizawa ya hana hajja qarasawa. " Fu'ad dai,d'ana fu'ad ". Da wani mahaukacin mamaki hajja ke bin maamah dake doka murmushi da kallo "Kinga Kalar surukan da ake fatan samu......wadanda za'a ciccibi juna....ba wadanda suke hangen turmusheka kai da mafarkinka ba.....maciya amana masu fatan kayi gyangadi su kafta maka sara.......zan shiga ciki in huta,ina da baqi anjima......idan kin gama ki rufe gurin.....karki damu kanki da lamarin laila......dama haka rayuwa take.....ka riqe dan wasu kaima a riqe naka,duniyar juyawa take haka da sauri........su madeena sun isheki zama.....ni kuma laila kadai ta isheni" Tana qarasa maganarta ta fara takawa zata fice 54 _Daga nana aisha RA tace,manzan Allah S A W yace: "anayin wanka akan abubuwa guda biyar,janaba....da wankan juma'a...da idan anyi qaho,da wankan mamaci(mutum ya yiwa gawa wanka)_ "Mariya!" Hajja da zuwa lokacin ta kasa riqe kanta ta kirata a hautsine "Koda wasa......koda tsautsayi kada kiyi tunanin cutar da laila......karki manta dukka sirrikanki a nan suke" Tayi maganar tana nuna mata tafin hannunta. Murmushi ta kuma sakar mata sannan ta juyo sosai tana amsata. "Wadannan sirrikan da kike da ganin sun isa abun tunqaho.....nabar miki su halak malak kiyi yadda kikeso dasu.....laila kuwa a yanzu mallakina ce,baki da hurumi a kanta,idan kuma kina ganin zaki iya to bismilla,ga fili ga me doki,kinsan dakin dana sanya aka sauketa ai" Ta furta tana nuna mata hanya,sannan ta juya hankalinta kwance tana fita daga dakin. ★k'arfe biyar da rabi yammacin ranar jerin luxury cars dinsa sukayi matsugunni a babban sashen ajiyar motoci na mansion House din nasa. Wani baqon abu daya kwana biyu baiyi ba,wato dawowa gida a lokaci irin wannan. Dawowarsa da wuri shine qarfe takwas zuwa tara na dare,wanda ita kanta matar gidan batasan lokutan dawowarsa ba. Kaman ko yaushe daga farfajiyar gidan ya tsaida kowa ya kuma sallami kowa,wanda kusan quarters ne guda daga can wani sashe daban na gidan da yawancinsu suke da nasu apartment din,ba lallai ma ka fahimci da wasu dake rayuwa cikin gidan bayan ainihin masu gidan saboda nisan tazarar dake a tsakaninsu. A hankali yake takawa zuwa ciki suna magana da farouq qasa qasa. "Na fita daga company,kuma ina tunanin sai gobe zan sak shiga......wani irin headache ne yake matsamin tun jiya......but daga dazun zuwa yanzu kaman ya qaru" "Dude.....kana over work fa?,Allow your self downtime......kana da aure amma a suna kawai......kasan benefit na aure kuwa da ba zasu qirgu ba?....Emotional support and mental health duka zaka samesu if ka bawa matarka damar shiga rayuwarka".... " Hey.....zaka fara ko?,waye ya gaya maka kowacce mace ake bawa dama ta shiga rayuwarka?,wasu matan poison ne fiye da yadda kake kimantawa,they are wicked" Ya fadi yana hadiye wani yawu lokacin da madaurin tunaninsa ya warware yana koma masa can shekarun baya.....sanda maamah ta zama silar rasa lafiyar mahaifinsu duk da kasancewarsa mutum ke kazar kazar,ta kuma zama silar barinsa sararin da suke kai yanxu suke rayuwa akai wato DUNIYA. Daidai sanda ta sauka daga saman high chair din data zauna a akai cikin kitchen din suna taba hira da ma'u,wadda take hada qullin wainar shinkafa zata soya musu "Bari na dauko na dawo" Tace da ma'u din tana gyara yafen qaramin Chantilly veil din data lullube sassalkan gashinta. Furucin nasa ya sanyata tsaiwa cak sanda muryarsa ta kaiwa kunnuwanta saqon da yake isarwa farouq,sai taja da baya tayi tsaye jikin qofar yana jiran wucewarsa don ta wuce itama zuwa dakin. "Let's try not to judge people and instead understand their perspectives". "Am not judging fa......dude ba zaka gane bane,na iso gida.....i need to rest.....call you later" "Okay byee" Farouq ya fada yana sauke wayar iska ya furzar daga bakinsa yana duban file din dake gabansa cikin katafaren kamfanin sarrafa kayan abincinsu dake sharada industrial area. Yanaji a ransa zai sake rage kwanakin tafiyar nan tasu ko wataqila hakan zai kawo kasuncin da yake fata tsakaninsa da ita. Yasha attempting saka amna cikin abun,yasan zatayi aiki sosai.....saidai kuma amna din quruciya tayi mata yawa,baisan ya zata dauki abun ba,uwa uba yana buqatar yayi komai cikin sirri. Shurun da taji cikin parlor din ya sanyata tunanin ya wuce,ta sauke siririyar ajiyar zuciya,kunnuwanta na maimaita mata da meye da meye ya fada akan mata?. Siririn tsaki ta saki zuciyarta na siffantashi da jerantashi cikin sahun mazan da sam bausan mutuncin diya mace ba....suke mata kallon kuma wata halitta da bata da wata daraja kwata kwata. Siririn tsakin daya sanyashi daga kansa a hankali daga rufe bottle na ruwan da ya tsaya ya bude yasha saboda yadda maqoshinsa ya bushe,yana ji kamar bazai iya qarasawa saman ba. Guri daya idanunsu suka hadu,ya kafeta da qwayar idanunsa da sukayi wani laushi tubus saboda yadda ciwon kan ke sara masa lungu da saqo na cikin kansa. A hankali ta zare nata idanun daga kanshi,sannan ta koma da baya zuwa kitchen din ba tare data qara koda second uku a wajen ba. Kansa shima ya dauke yana ajiye robar,sannan ya soma takawa a nutse yana wucewa ciki kafin ya haura zuwa saman. Tun daga wancan ranar bai qara ganin gilmawarta ba cikin gidan,wasu lokutan ma sai yaje gaida anni ta tambayeshi iyali take fado masa a rai. Wani irin mummuna fito na fito yayi da kansa akan damuwa da abinda tayi masa a ranar din,yana ganin bai cancanci ya sanya damuwarta a ransa har haka ba.....sai ya sake qarawa kansa wani busy din akan wanda yake ciki,yana saka ran wannan ya zama silar mancewarsa da komai,wanda yawan ayyukan da suka zarta qa'ida din daya azawa kansa yake kyautata zaton shine silar wannan ciwon kan da ya fara fama dashi. A gajiye da wani irin bacin rai da baisan meye dalilin faruwarsa ba daga shigowarsa gidan ya dinga zare suit din jikinsa yana zubarwa,duk da cewa ba al'adarsa bace hakan. Bathroom ya wuce kai tsaye,ya hada ruwa me dumi da zai dace da yanayin sassanyar iskar dake kadawa,wanda asalinta hadarine daya hado,bai saukar da ruwan ba,amma ya canza kala zuwa ruwan toka,ya kuma bada iska me sanyin dadi dake busawa da qamshin qasa,yanayin da yake bada tabbacin anyi ruwa a wani gurin kusa da kano. Mintuna kusan arbain ya fito daure da towel,gargasar jikinsa dama sumar kansa duka sun jiqe da ruwa. Faffadan qirjinsa dake lullube da gargasa ya fara gogewa da towel din yana isa gaban madubi,daidai sanda yaga wayarsa na haske. Kaman ya share saboda bayason doguwar magana,amma koda ya duba yaga maamah ce sai ya zamana bashi da wani zabi daya wuce ya daga kiran. Sai daya zauna saman bean bag chair din dake ajiye a gefe sannna ya daga hade da sallama. "Barka da yamma" Ya dora da fada yana lumshe idanunsa saboda yadda kansa yake sarawa. "Barka kadai......kana office ne?,inason ganinka idan kun tashi,akwai muhimmiyar magana da zamuyi da kai,sannan akwai baqi da sukeson ganinka" Ta fada kanta tsaye. Yatsun hannunsa da baya riqe da wayar ya cusa cikin sumarsa,yanajin yadda ta jero buqatunta kai tsaye ba tare da neman jin uzuri ba.....ya ya wuni?,akwai damuwa?,yana da lafiya ko babu?. Baisan sai yaushe wannan dabi'ar tata na damuwarta itace kadai damuwa zata sauya ba.....baisan sai yaushe zata damu da damuwar wani ba ta aje tata damuwar da son kan a gefe ba. "Bana company na dawo gida....." "Okay,to ya za'a yi kenan?,don duk yadda za'ayi inason ganinka lallai lallai a yau din,ko meye kakeyi ka katseshi kazo ka sameni" Ta sake fadi da dukka sautin da zai gaya masa da gaske take. Jaririyar ajiyar zuciya ya sauke yana cire yatsunsa daga sumar tasa "Ciwon kai nake maamah.......amma zansha magani na kwanta zuwa anjima zan shigo" Ya fada da raunanniyar murya,yana jin har qasan ransa ya rasa wani part me girma a rayuwarsa,yanajin ya rasa wani abu me matuqar muhimmanci a rayuwarsa. Duk da yana da anni,yana da farouq,yana da saddiq da musaddiq,amma lokuta da dama yana jin kamar shi kadai ne.....yanajin kamar shi kadai yake rayuwa a duniyar,wani irin maraici da kadaici yana mamayarsa. "Allah ya kaimu,kada kayi dare da yawa Allah ya sawwaqe" Ta hade maganar duka lokaci guda. Ya jima idanunsa saman wayar yana kallonta,zuciyarsa na tuna masa abubuwa da dama ciki harda abbansu. Tun asali shike damuwa kuma shike kasa bacci idan dayansu baida lafiya,koda ciwon baikai ya kawo ba. Tun da can ita din bame damuwa da lamuransu bace,tafi damuwa da duk hanyar da zata maida taro ta koma sisi. Sai daya bushe tas bai sani ba kafin ya miqe yana isa ga walk-in closet dinsa,boxer kawai ya zura bayan ya mulke jikinsa da cream dinsa,ya kuma shafe jikinsa da turarukansa,sai ya koma gefen gado ya zauna bayan ya balli wasu tabs na saukar da ciwon kai ya sha,ya dauki remote guda uku,daya ya zuge duka labulayen dakin dashi,daya ya kashe hasken duka fitilun dakin banda ta gefen gadon,dayan kuma ya saisaita sanyin ac din yadda zai daidai da yanayin da yake ciki. Cikin duvet ya shiga ya duqunqune yana lumshe idanunsa gami da sauke nannauyan numfashi,ya lumshe idanunsa yana son fatattakar kowanne tunani da lissafe lissafe ko zai samu brain dinsa tadan huce. Ana kiraye kirayen sallar magariba ya farka daga gajeran baccin daya daukeshi,yaji dadi sosai a jikinsa,sai ya wuce toilet yayi tsarki ya daura alwala. Masallaci ya wuce kai tsaye,akayi magariba da ishai duka dashi,sannan ya dawo ya shirya cikin tattausar exclusive Morocco ta maza me zuwa hade da wandonta. Kalar royal blue ce,sai akayi mata ado da gold zare daga wuyanta hannu aljihu qasan wandon da tsagar gefe da gefe na rigar. Wata zagayyar hula ya dora saman kansa ruwan gold din,wanda yawanci yankin larabawa su sukafi ta'ammali da ita,take farin bafullatanin nan muhammadu jikan jadda ya fito da wani irin kyau da zai wahala ka kalleshi sau daya ka kauda idanu (Niko nace uhmmmm,kaman kuwa yasan zance akazo yi gurinsa😂). Clogs ya sanya gold color,ya feshe jikinsa da mayen turarensan nan dake saurin kama zuciya. Key ya laluba a ma'ajiyarsu ya dauki spare key din daya daga cikin motocinsa. Yau din da kansa yake sha'awar yin driving,abinda ya jima rabonsa da yayi. Yanason ya shaqi fresh air dinnan shi kadai ba tare da wani a gefensa ba wai da sunan yana kare lafiyarsa ba. Ta kammale komai a daki kaman yadda ta saba duk dare,wanda idan ta shiga kuma ita da fitowa koda hallway ne sai kuma da safe. Tun wancan ranar ta sake jin ta tsani dukka wani abu da zai sake hadasu ko ya hada alaqarta dashi. Idan ta tuna tambayarsa din kuma takanji wani mugun haushinsa na sake mamayarta,tana jin a sannan me yasa bata amsa masa da eh wajen wani naje ba?. Sai data zauna tsaf sannan ta duba night stand fridge dinta babu ruwa ko qwaya daya a ciki. Baida girma fridge din,don haka kadan kadan take saka ruwan saboda gorar zata cika waje. Miqewa tayi tana yamutsa fuska,ta dauki Indonesian hijab dinta navy blue ta zura wanda ya haskata matuqa,ya kuma fidda lallausar sumar dake kwance gaban goshinta. Harta miqe ta dauki wayar huda da zuwa yanzun tayi nisa da amfani da ita,tayi playing drama din da take kalla daga inda take,a haka ta fita rabin hankalinta yana kan wayar. Wannan dalilin ya sanya bataji saukowarsa ba daga stairs din saboda lallausan clogs din dake qafarsa baya bada sauti ko kadan,duk kuwa da cewa da dan sassarfa yake saukowar yana gaggawar isa ga mota,so yake yaje ya dawo da wuri akwai ayyukan da bai samu daman yi ba dazu,yanaso ko cikin daki ya ragesu. Stairs din ya danyi kwana kadan wanda sai kazo rabi sannan zaka hangi wanda ke fitowa daga farkon hallway din,kaman shima......sai daya zo rabi sannan ya ganta. Idanunsa suka sauka saman fuskarta data fita fes cikin tsakiyar hijabin kalar luxury Morocco din jikinsa. Hasken dake fitowa daga cikin wayar ya haske fararen idanunta dake sheqi kamar an diga mai. Bai fasa saukowa ba kaman yadda taci gaba da takawa idanunta kafe akan wayar,har sai da cikin jikinta taji kamar ta iso qofar da zata sadata da parlor din. Daga kan da zatayi ta tsinceta dab dashi sanda yake stair din qarshe. Sai ta juya a hankali da zummar yi masa yadda ta saba wato komawa don ta kubcewa hada numfashi dashi. 55 _Daga abu hurairah RA yace,manzan Allah S A W yace: "ku kashe baqaqe guda biyu koda kuna cikin sallah; MACIJI DA KUNAMA_ Taku biyu kacal tayi ya cimmata,ya kuma sanya hannunsa ya dawo da ita baya,sai gata tsaye cak a gabansa kaman ba inda ta matsa. Idanunta tsakiyar nasa idanun da suka qaa girma kadan saboda ciwon kan dazu,yayin da hucin numfashinsa ya dinga fita cakude da qamshin turaren jikinsa yana kaiwa ga hancinsa. "Wanne kalan dodo ne ko abun tsoro a jikina da kike gani?" Ya jefa mata tambayar a zafafe yana ware mata idanunsa. Ja baya tayi niyyar yi da sauri saboda yadda ta dan tsorata kadan da yadda idanun nasa suka qara girma,ga wani shimfidadden kwarjini dake fita daga cikinsu ya daki zuciyarta lokaci guda ya kuma ninka gudu da bugun zuciyartata. Hannunsa qwaya daya ya sanya yasake dawo da ita gabansa yana sake bude mata girman dukkanin idanunsa. "Ki nunan abinda ke baki tsoro a jikina nace!" Ya fada da dan tsawar takaicin abinda takeyi masan. Shi tun farko mutum me dan kai tsaye,koda laifi kayi masa yafison ka fuskanceshi kai tsaye.....haka koda matsala kake dashi yafiso ka tunkareshi kai tsaye ku warwareta. So take ta maida masa me zafi ko zata fanshe abinda ya gaya mata ranar nan,amma sai ta lalubi kwanyarta da bakinta tsaf ta rasa komai kamar an mata sata. Ringing din wayarsa ne ya sanyashi maida dubansa ga wayar. Kusan a tare idanunsu suka kai kai,kuma daga shi din har ita sunga sunan da yake rubuce a kai FAREEDA KHALED MUSTPHA. Maida dubanta tayi ga fuskarsa ba tare da tasan dalilin hakan ba,sai kawai ta zabi ta zille ta tsakanin qofar ragon da yayi mata,saidai kuma tana motsawa kamar hankalinsa yana maqale ne a jikinta ya daga kai ya watsa mata idanunsa bayan ya maida wayar aljihu ya sakeyin kicin kicin da fuska. "Daga yau duk ranar da kika qara ganina kika koma kaman kinga dodo saina biki har cikin dakin na zaneki tas ciki da baya". Maganar tayi mata banbarakwai,kamar wata nadra ko haneefa?,wannan mamakin ya bayyanata tsakiyar qwayar idanunta da baisan me yasa yake yawan sanya nasa idanun a cikinsu ba duk sanda magana irin haka ta hadasu. "Kina mamaki ne?,ko kina ganin kin wuce duka?,ki gwada koda gobe ne ki gani.....and,daga yau kada ki sake ganina baki gaidani ba......tunda ko banza ana ci dake ai ko?,koda ban baki abinda wadancan suke bakin ba" Ya qarashe maganar yana sakar mata hanya. Cikin qasa da second uku ruwan hawaye ya tararwa idanunta,ya za'ayi ya qara mata ciwo akan wancan ciwon,tana jin lallai yau ta barshi ya tafi haka yaci bulus din da ba'a taba cinta a kanta ba "Ka daina burga kaman kana da abun bayarwar.......ni bana buqatar ragowar su fareeda tunda akwai masu fresh......." Cak maganar ta tsaye mata a maqoshi sanda yayi wani irin waiwayowa daidai sanda yake dab da zarcewa falon. Batasan ta juya ba har ta soma tafiya zuwa dakinta ba sai da taji tana taka lallausan carpet din dake shimfide daga tsakiyar wajen. Dif wuta ta dauke masa,zuciyarsa ta shiga raya masa nau'ikan hukunci mafi tsauri daya dace yayi mata. Saidai kiran wayarsa ya sake katse masa duk wani hanzari,ya duba kiran a fusace yana tunanin fareeda ce,amma ganin maamah ya sanyashi tattare duk wani bala'i daya taso masa ya hadiyeshi,sannan ya daga wayar yace da ita a taqaice "On my way" "To ka hanzarta" Maamah ta fadi tana jin dadin yana hanya bawai yaqi amsa kiran nata bane. Kai ya jijjiga yana takawa a hankali yana ficewa,saidai a ransa yaci alwashin dole ya ajiye mata abun tunawar da bazai sake fadin magana ta maida masa ba. Duka duka shekarunta nawa amma sanadin aure raini yana neman shiga tsakani?". Ya fada qasan ranshi sanda yake tayar da motar. Da wani irin speed yake jan motar,wanda dama sabonshi ne gudu a mota,ba tun yau ba ba kowa ke iya shiga mota ba indai shine zai tuqa. Idonsa ya lumshe yana tuna abinda tace masan,sai wani sashe na zuciyarsa ke gaya masa.....zai wahala cikakkiyar budurwa me kunya ta iya fadin hakan.....ita kuwa bata cikin kowanne sahu,dom haka idan ta fadi sama da haka ma fuad kada kayi mamaki.....kowa yasai rariya yasan zata zubda ruwa. Har ya isa gidan maamah wannan kalmar ta kasa fita a ranshi "Ragowar su farida....kamar ma kana da abun bayarwar" Har cikin ransa ya gamsu ta rainashi,sai ya samu Kansa da kallon Kansa a side mirror,yana tuna dararen da yake kashewa a tsaye ba tare daya isa ya kwanta ba bare ya samu cikakken bacci saboda tsananin yadda ya kame kanshi. Da wannan bacin ran,da kuma tunanin hukunci mafi tsananin daya kamata ya dauka ya isa parlor din maamah. Mamaki na gasken gaske ya cikashi lokacin da yayi sallama ya tsinci fareeda cikin masu amsa masa sallamar tasa. Tana zaune hankali kwance saman sofa din parlor din. Sanye take da riga da wandon Palazzo daya bude sosai daga qasa. Rigar me gajeran hanny ta lafe a jikinta ta kamar yadda Palazzo din ya fidda shape din hips din ta zuwa qugunta. Bandana ce kawai saman kanta,hannunta riqe da wayarta. Kallo daya tak ya mata ya dauke kansa kai kace bai taba sanin wata halitta a duniya me ire iren kama da ita ba. Qasan maqoshinsa kuwa kawai kaiwa da kawowa maqogoronsa yakeyi,adams apple dinsa yana motsi daga sama zuwa qasa,ya taka a nutse kuma kai tsaye ya wuce gaban maamah din a ladabce. Tunda yayi sallamar ya shigo taji gaba daya an tsinke duk wata jijiya daka iya baiwa dan adam kuzari daga jikinta. Tunda take haukan son fuad bata taba tunanin haduwarsa da kyansa ya zarta yadda ta gagganshi bama sai yanzu data ganshi cikin shigar mutanen Morocco,wanda nan Nigeria zaka ga suna kama da tufafin da sarakuna ke sanyawa musamman idan suna ganawa da baqi cikin gida. Numfashinta cak yaso tsayawa,muhammad fuad ya wuce yadda take hangensa a nesa,a take taji tabbas zata iya sadaukar da komai data mallaka don ta samu fuad din a matsayin mijin aure (Anya....fuad din fa me tsada ne......amma muje zuwa,tunda kin kama maamah wataqila kina da rabo). Kusan duka gaisuwar da sukayi shida maamah da gajeriyar gabatarwar da maamah tayi masa bata ji ba "Baquwar taka ce muhammadu.......ina me umartarka ka saurareta ka kuma fahimceta.....duk wanda yayo tattaki qafa da qafa ya taho gareka saboda yana sonka ba qaramin masoyi bane,idan Allah yaso kuma matarka ce" Ta fadi maganan qarshe tana yunqurawa ta miqe. Daga kai yayi yana duban maamah sanda take jifan fareeda da murmushi,da salo kuma na bada goyon baya take cewa "Gashinan fareeda,bari na shiga na fito kafin ku gama" _idan Allah yaso kuma matarka ce_ yaji amsa kuwwar maganarta ta qarshe tana nanata kanta cikin kunnuwansa. Maganar sai taso ta masa kama da maganar data masa daidai sanda ta tilastashi auren waccar yarinyar.......me yake shirin faruwa?.ya tambayi kansa. "It will never happened" Ya fada yana qaryata komai da zuciyarsa ke qiyasta masa zai iya faruwa. "Hi......ka ganni har gida?,yanzu ka yarda garin masoyi baya nisa ko?" Ta fada tana sakar masa murmushi,murmushin nata dake daidai da diban garwashin wuta ta watsa masa. Wannan bai dameta ba,yanayin fuskarsa duka bata sakashi a mizanin damuwa ba.......zai gata ta zame tana saukowa qasa. Ta qaraso dab dashi tayi Zaman raquma tana dubansa "Please Muhammed kada kayi rejecting dina.....na maka alqawarin zame maka duk kalar matar da kakeso kake buri" Ta furta da tsananin narkewa. "Stop it please......ke me yasa baki nemawa kanki martaba mutunci da kima?". Ya fada bayan ya daga mata hannu ya dakatar da ita daga maganan farko launin idanunsa sun fara sauyawa saboda bacin rai. A rikice ta girgiza kai ganin yana juye mata zuw wannan fuad din me wahalar samu.....wannan fu'ad din me tsananin tsauri "Mutunci martaba da kima duka susha zamansu muddin zan samu muhammad fuad". Shuru ya ratsa qarshen maganarta,ya xuba mata ido yana sansano alamu alamun hauka tattare da ita,sai ya matsar da fuskarsa kusa da tata kadan,da wani sauti can qasa wanda tsanantar bacin rai da kuma sarawar da kansa yayi ya dawo da ciwonsa sabo fil ya tilas masa maganar a haka yace "Gashi shi kuma muhammad fu'ad din saida wadannan abubuwan ake samunsa......." Daga haka ya miqe tsam da zafin nama,sai gata ta miqe tare dashi cikin tsoro da fargabar kada yaqi tsayawa ya saurareta duk da kuwa ta dangana da mahaifiyarsa. "Umarni nake baki......ki tattara kayanki kibar gidan nan,kada na dawo jibi na sameki,don gobe ma tayimin kadan,bazan iya shaqar iska a wajen da kika dade a cikinsa ba". Yana kaiwa qarshe ya juya da zafin nama me gauraye da fushi ya soma fita. Ta dauka zata jure saita kasa,ta bishi a baya da gudu gudu tana kiran sunanss,saidai ko ta kanta baibi ba,ya bude motarsa ya shige ya kunna ya tasheta da wani irin qarfi ya fusgeta yana fita a gidan,don ko sanda ta qaraso sawayen motar kawai ta samu,saita zube a wajen tana qwala kiran sunansa,abinda kunnuwan maamah suka jiye mata kenan,ta fara saukowa da sassarfa daga sama. Baisan yadda yakai kanshi gida ba saboda tashin hankali da tsananin ciwon kan daya saukar masa,shidai yaji daya daga cikin security nasa na cewa yabar motar daga nan zai qarasa shigo da ita ya gyara parking din. "Sai yaushe maamah zata canza?,sai yaushe zata zama cikakkiyar uwa?,sai yaushe zata zabi girma da mutunci sama da kudi?,sai yaushe?,sai yaushe?". Kusan wannan shine abinda ya sanyashi kwana ya kuma tashi da ciwon kan daya hanashi fita,ya kuma kashe dukka wayoyinsa don baya qaunar ya nemi wani ko shi a nemeshi. *_WASHEGARI__* *_BAQIN DARE_* *_MUHAMMAD JADDA RESIDENT_* *10:45 NA DARE* Tunda ta fara kallon film din hankalinta bai kwanta ba sai yau da taga qarshensa. Duk da cewa ya bata mata lokaci sosai,don sai a yanzun sha daya saura na dare ta kammala......amma kuma ya haifar mata da wani irin nishadi a zuciyarta,nishadin da duk idan ta tuna yadda rayuwar stars din ta kasance a ciki sai taji ta saki dan murmushi kadan. Sam ita din ba ma'abociyar kallo bace......wannan shine film na farko data fara kara full kuma wai korean series. Idanunta ta lumshe tana shaqar iskar dake kadawa sosai take kuma yiwa kanta hanya ta windows din dakin da yawanci yakan barshi a bude saboda samun fresh air da tafi iskar ac artificial air dadi a wajenta. Gabanta yadan buga kadan,tayi kuma hanzarin bude idanunta sanda taji kaman motsin taba window din. Ta tsaya cak daga qoqarin fidda rigar jikinta da takeyi,tsahon mintuna biyar bata sake jin komai ba,saita matsa gaban windows din dukansu,ta bisu daya bayan daya ta zugesu,ta kuma sanya musu lock. "Sabreena kin zama matsoraciya" Ta tsokani kanta da kanta,ta kuma sakarwa kanta da kanta din murmushi. Ita kanta batasan yaushe ta koma hakan ba,saidai girman gidan koda rana ce ta take tsoro yake bata,duk da tassn cike yake da security musamman idan ma'u ta gama kai kawonta ita da ameh kowa ya wuce gefansa. Towel ta daura babba,har zata wuce toilet din taji kaman yau garin da iska,don haka ta miqa hannu ta dauki hijab din da tayi salla dashi ta zura a jikinta ta wuce bandakin. Tana wankan amma kadan kadan takejin gabanta yana faduwa wanda ita kanta batasan dalili ba. Yau din sai ta samu kanta da rage tsahon lokacin da takan dauka a bandakin,cikin qasa da mintuna goma ta kammala,tayi brush ta busar da kanta,sannan ta daura towel din ta maida hijabinta ta fara takowa tana fitowa. Sanda ta dora hannunta akan handle din gabanta ya sake yankewa ya fadi. "Hasbiyallahu wa ni'imal wakeel" Ta furta a hankali kaman yadda yanzu yadan fara zama a jikinta,don cikin jadawalin karatunsu da rumaisa akwai azkar sosai da addu'o'i masu yawan gaske. Jiki a sanyaye ta murda handle din ta jawo qofar ta bude sannan ta fito,kai tsaye ta soma nufar madubi. Abun mamakin yadda takejin baqon qamshi cikin dakin,tadan tsaya kadan tana buda hancinta still qamshin takeji,sai kuma tunanin iskar dake ratsowa ta cikin rufaffun windows din qilan ke debo qamshin daga waje zuwa dakin,don haka hankalinta kwance ta qarasa gaban mirror din tana duba fuskarta da jiya taqi wani qurji qwaya daya ya fito mata. Wutace tsaf ta dauke mata kafin wata mahaukaciyar faduwar gaba ta rufto mata,tun daga saman kanta har zuwa yatsun qafafunta da ganin fuskar dake tsaye a bayanta. Dagawa qirjinta ya shiga yi daga sama zuwa qasa cikin wata irin razana da takejin kamar tana shirin dimaucewa ne......sake matsota yakeyi idanunsa cikin nata,kaman yadda fuskarsa ke shimfide da shu'umin murmushin nan data saba gani a fuskarsa a shekarun baya. "Mmmm........." Ta dinga yunqurin fadin sunansa,amma sai taji kaman an sanya gum an manne labbanta na sama da qasa guri guda. *_TOFA!_* *_WAYE WANNAN?_* *_NACE WAYE WANNAN?_* *_MUHAMMAD FU'AD NE DA KANSA?_* *_KO KUMA WANI MUTUMIN NE NA DABAN?_* *_TURQASHI_* *_Allah yasa muna cikin masu rabon ganin ranar litinin lafiya_* *_karku yadda karki yarda aci gaba da sukuwa da zamiya cikin labarin nan ba tare dake ba_* *DA SAURAN KALLO!!!* Tofa nayi qarqaf😂😂 Allah ya bani ikon baku na ranar monday🙏🏽🙏🏽🙏🏽😂 56 _Daga ummu habiba uwar muminai Allah ya qara yarda a gareta tace,naji manzon Allah S A W yana cewa "duk wanda ya sallaci raka'a sha biyu daga rana zuwa dare(bayan sallar farillai guda biyar),Allah zai gina masa gida dasu a aljanna_ _muslmin ne ya rawaito_ _raka'o'in nan sha biyu sune,biyu kafin asuba,hudu kafin azahar da biyu bayan azahar,biyu bayan magariba,biyu bayan isha'i saiki qara da wuturi_ _Sannan akwai hidisi me zaman kansa abdullahi bin umar ya rawaito,manzan Allah S A W yace ALLAH KA YIWA BAYAN DAKE SALLAH RAKA'A HUDU KAFIN SALLAR LA'ASAR RAHAMA_ *_IBADA DUK IBADA CE,AMMA MAFI SOYUWAR AIKI A WAJEN ALLAH DUK QANQANTARSA SHINE WANDA ZAKA DAWWAMA KANA YI,SAIKA DAUKI WANDA KASAN ZAKA IYA DOREWA_* Tana kallonsa ta cikin madubin yana ci gaba da kusanto inda take,saidai gaba daya ta kasa motsa koda yatsanta ne ballantana tayi tunanin abu na gaba daya kamata ace ta aiwatar. Shu'umin murmushinsa da kallon da yake dubanta dashi duka ba wanda ya fasa,yaci gaba da kusantota kowacce gaba ta jikinsa tana jin wani shauqi tare da dokanta ta sadar da kanshi gareta. Irin yadda ya fitinu da ita ba abu bane me sauqin fassarawa ba......sai kuma gashi a bagas zaice ko a banza wata hanya ta samun isa gareta ta riskeshi cikin sauqi,wanda zai iya kiran hakan da qatotuwar sa'a cikin rayuwarsa. "Mashkur!" Ta fusgi sunan da hanzari ta kirashi a tsawace bayan ta maimaita la'ilaha illa anta subhanaka inni kuntu minazzalimeen har batasan adadi ba. Tsaiwar da yayi ita ta bata damar waiwayowa da wani irin hanzari kamar wadda aka fusga. Idanu ta zuba masa kaman yadda shima idanun ya zuba mata yake kallonta da dukka iyakacin kallonsa. "Me ya kawoka gidan mutane?......har dakin matar aure?" Ta fadi da wata irin birkitacciyar murya data cika da razani da tsoro. Wata irin dariya ya qyaqyace da ita,harda komawa ya fada saman gadon nata,sannan ya tashi ya miqe yana fuskantarta. Ya bude baki zaiyi magana a hankali sautin saukar ruwan saman farko ya baqunci kunnensu,shatin ruwan ya fara sauka ta glass din windown dakin sai ya saki murmushi yana dawo da dubansa kanta. "Kin gani ko?,.....ko Allah ma yana sona......ko Allah ma yasan kin cuceni....kuma ko Allah yasan kedin azzaluma ce,wannan zubar ruwan shi zai sake toshe kunnen duk wani da kike tunanin zai ceceki ko zai kawo miki dauki,duk da kuwa wannan ginin gidan naku dama kaman anyishi ne domin ni,yana riqe sirrin kowanne motsi yadda ya kamata". Ya fada yana kallon yanayin roofing na dakin yana sakin murmushi. "Nayi mamaki wai da kike tambayata abinda ya kawoni,bayan akwai basussuka na da yawa a kanki?". "Mashkur ka haukacene?,kasan gidan waye ka shigo?,gidan matar aure har tsakiyar dakin aurenta..... " Fara takowa yayi yana sake nufota yana dariya "Ina cikin gidan muhammad fu'ad jadda,the owner of jadda diamondchore resources.......sannan ke din sabreena ce,mata a wajensa.....bayanin yayi daidai?" Ya jefa mata tambayar yana dage mata dukka girarsa biyun bayan ya tsaya daga takowar da yakeyi. "Ko kina buqatar wani qarin bayanin?......kinaso ne na gaya miki da license dina na shigo gidan nan?,da license daga hannun wata mace mafi kusanci da me gidan?". Daukan tunaninta yayi ya luluqa wajen lalubar ma'anar abinda yake fada,da license daga hannun wata mace mafi kusa da me gidan?,wace kenan?. Kaman yasan abinda take tunani a kai yace "No dear......kada ki wahal da kanki wajen tunanin wace..... Ki bari na gama kashe qishirwata sosai sannan mu zauna mu tattauna..... I need you.....na azabtu da yadda asara biyu ta fadamin......babu ke ba kudina......come please" Ya furta yana kawo mata cafka. Batasan tana da tsananin zafin nama har haka ba sai data kufce masa ya kama iska. Sukabi hannunsa da kallo dukka su biyun shi da ita. Shi dariya ya saki yana jijjiga kai "Kada ki dauka kedin me sa'a ce ko da yaushe.......idan a wancan karon kin kubcemin...... Na rantse wannan karon baki isa ki kubuta ba,koda kuwa a gaban mijinki ne a yau sai na kashe qishirwar dake raina" Ya furta yana daga rigarsa,take ta hangi hancin bindiga daga aljihun trouser dinsa. Kaman an debo bulo an jibga mata haka taji wani matsanancin tashin hankali ya keto mata,bata gama sauke abinda ya taso mata ba ta ganshi ya taso mata yayo kanta gadan gadan. Wani irin qarfi ne yazo mata,ta tattara hijabin jikinta da batakai ga cireshi ba da kyau ta haura sofa bed din dake gabanta ta wuce tsakiyar gadon "Ka fita min a gida.... Ka fita tun ban tada security din gidan nan ba" Ta fada tana duban sashen da wayar girke take a dakin wadda zata baka daman kiran kowanne sashe na gidan. Ta shiga shock sosai sanda ta lura ya gutsire wayar gaba daya ya fasa kan,duka yaushe yayi hakan da ko alama bataji ba. Dariya ya saki yana cewa "Kinga abinda ya samu telephone din ko?....." Bata bari ya qarasa ba ta tattara dukkanin qarfinta ta kwarara ihu tana fadin "Wani ya taimakeni" Abinda ta dinga maimaitawa kenan har sai da taji maqoshinta yana wani suya da radadi. Dakatawa tayi hawaye suna cika idanunta,tana duban mashkur dake qyaqyata dariya. "Zan iya qara miki lokaci kici gaba da ihu......kiyita ihu har iya yadda kikeso". "Fuad!. ....fuad!!!!" Ta sake qwalawa kiran sunansa. Karo na farko da ta fara ambatar sunan nasa kenan. "Yana can yana bacci" Ya fada yana juyi kaman zai taka rawa "Na sakashi bacci,kuma bazai tashi yanzu ba,sai na gama hutawa da matarsa" Ya sake maimaitawa cikin yanayin nishadin da kana kallonsa zakayi imani yakai masa har qasan zuciyarsa nishadin da yake ciki. "Mashkur,........ka saurara haka,ya kamata kasan kuskure kake tafkawa ba qarami ba.......ketawa matar aure haddi mashkur?!" Ta furta a tsawace. Dariyar nishadi ya saki yana kallonta,ya kama button din rigarsa ta saman ya fara ballewa yana zareta ya yar. "Kada kiyi kaman bakisan komai ba.......kina tunanin yaune na farko dana fara kwanciya da matan aure?,na kwanta dasu har bansan adadi ba......kawai ke dince ta daban,kin kasa fita a raina......bazan miki qarya ba,koda na dandana yadda kike banajin zan iya ci gaba da rayuwa ba tare da ke ba......shawara daya kawai zan baki,kada kiyimin gaddama.......ki bani kawai salin alin don na tabbatar kinsan komai,ba wani abu baqo a wajenki" Sasai kalamansa sukayi mata nauyi a qirji,ta tabbatar inda za'a tsaga jikinta ba za'a taras da jini ko digo ba saboda tsananin tsoro da fargici. Ranta yakai maqurar baci sanda taga yana yunqurin haurowa gadon "Har ka mutu mashkur ba zaka taba samun komai daga gareni ba.... Ko gawata tafi qarfinka mashkur bare gangar jikina a sanda numfashi yake busawa". "Well.....tunda kin zabi muje ta haka dake!" Da furucin da haurowarsa saman gadon duka lokaci guda suka faru. Wani tsalle tayi da zummar barin gadon,saidai kuma ya samu nasarar take qasan hijabinta da qafarsa ganin zata kufce masa,abinda ya sanyata data dira din bata sauka a daidai ba,hannunta ya daki side bed ya bada wani irin qum. Qara ta saki cikin tsananin azaba......azabar da bata hanata ci gaba da qoqarin qwatar kanta ba,cikin sa'a santsin bedsheets din dana hijabinta suka sanyashi ya zame zaman lallausar katifar,saita miqe itama,amma ta kuma zamewa take fuskarta ta bugi gefan bedside din still. Bata damu da radadin daya sake ratsata ba.....sake miqewa tayi tana harin qofa,abinda ya lura dashi kenan shima ya miqe da azama,tana isa qofar shima yana qarasawa sanda take kici kicin bude key din,ta finciketa ya watsar ya saka key ya kulle qofar. A zafafe yabar bakin qofar yana nufar qofar toilet yana cewa. "Yau zaki gane waye mashkur.....tunda baki zabi komai ya kasance ta hanyar maslaha ba" Key din jikin qofar toilet din shima ya murza ya kulle,tana kallonsa sanda take qoqarin sake tashi saboda buguwar da tayi a hannu da fuska,yadan bude window din waje ya watsa Keys din sannan ya sake waiwayota. "Kaji tsoron Allah mashkur......kada ka keta haddin aure.......da auren wani a kaina.......ba bazawara ko budurwa bace!" "Allah yasa tattabara ce ke" Ya fada cikin rashin damuwa yana durfafota da sassarfa kaman me wasan motsa jiki. Cafka ya sake kawo.mata ta sake samun nasarar gocewa abinda ya sake qona masa rai,sai kawai ya zabi ya galabaitar da ita.....don duka alamu sun nuna masa cewa gwana ce wajen iya zilliya,kada ta bata masa time ta kuma bata masa plan,don haka yakai mata naushi. Ya sameta ta kafadarta ne yayin da nashi hannun ya wuce ya daki bango,abinda ya sanya wata azaba me tsanani ratsa kwanyarsa. "Ouch!" Ya fada cikin tsananin jin zafi,yayin da zuciyarsa ta sake tunzura "Ni xaki sanya naji rauni?". Yana kaiwa nan ya shammaceta yakai mata qafa ya kwasheta,take ta fadi ta bugu da qasa. "Wayyo Allah na" Ta fada cikin tsananin radadi tana riqe qugunta gami da runtse idanunta. Wannan shine abinda ya bashi daman isowa gareta,ya kama bayan kanta inda ta tattare gashinta tayi gammo dashi ya riqe gam. Wata azaba ta ziyarci tsakiyar kanta zuwa qwaqwalwarta,ba shiri ta sake qwalla qarar da zuwa yanzu ta yanke tsammani akwai me cetonta. Yana riqe da kan nata ya turata har saman dressing table dinta,baiyi wata wata ba ya buga goshinta samanshi,take goshin nata ya fashe,saidai kuma tana dagowa ta dago da bedside lamp da akayi ado da ita saman mirror din ta kwatsa mata ita tsakiyar kanta,abinda ya sanyashi sakinta ba shiri yana dafe da wajen. Duk da wajen bai shafe ba amma take yayi wani malulu azaba ta shiga ratsashi tako ina. Ya kalleta sanda jini ya fara diga jikin sky blue din hijabinta yana jin wani fushi mara misali yana saukar masa. Bai taba tunanin zaiyi minti biyar ba daga sanda ya shigo dakin ba tare daya samu galaba a kanta ba,sai gashi yanzu wankin hula yana neman kaishi dare... 𝐃 𝐔 𝐍 𝐈 𝐘 𝐀 𝐓 𝐀 _Zafafabiyar_ ̶B̶O̶O̶K ̶2 ⱧɄ₲Ʉ₥₳ 𝙋𝘼𝙂𝙀 57 57 _Daga abu hurairah RA yace,manzon Allah S A W yace "mafi falalar sallah bayan sallar farilla itace sallar dare_ *_ga falala ga kaifi,biyan buqata kaman yankan wuqa😄,Allah ya bada ikon jurewa_* Ga mamakinta sai taga ya samu waje ya zauna yana mulmula wajen. Tsahon mintuna tana tsaye tana kallonsa tana dafe da inda jinin keci gaba da diga bata da abun tareshi. Ko na minti guda taqi yarda ta dauke kallonsa a kanta gudun kada ya mamayeta bata shirya ba. Hannun nasa ya sauke,ya fidda kwalin wiwi,ya zari guda biyu ya kunna musu ashana sannan ya sanya duka biyun a bakinsa ya soma zuqa cikin gwanancewa. Yadda ya tsara zaiyi da ita sai yaji me yasa bai taho da kayan mayensa ba?,ko banza yafi samun kalan nishadin da yakeso?,ya yanke ya fara zama yasha wiwi dinne don yadan huce kadan ta yadda zaifijin gardin abun. Tunda ya kunna wiwi din hankalinta yayi mummunan tashi. Ta san tabbas zata shiga wani mummunan yanayi ne da idan batayi wasa ba xai galabaitar da ita. Asthma dinta,ba kalar hayaqin dake saurin tayar da ita irin hayaqin wiwi taba da shisha. Matsawa baya ta dinga yi tana duban yadda hayaqin ya fara gauraye dakin,yana canxa yanayinsa daga ainihin qamshi xuwa gurbataccen warinta maras dadin shaqa. Dukka hijabin ta cukuikuyeshi tana rufe hancinta dashi,a hankali tana jin yanayinta yana son ya fara sauyawa. "Zaki fahimci abinda ake nufi yau da asalin fyade" Kamar mugun dawa haka ya miqe zumbur ya kuma nufota,ta juya itama da nata hanzarin da nufin barin gurin,saidai tuni ya miqa hannu ya danqo hijabinta ya dawo da ita gabansa tana fuskantarsa. Yadda take qoqarin toshe hancinta a nasa tunanin ya karanci batason warin wiwin ne,don haka ya zuqeta sosai ya kuma soma fesa mata ita saman fuskarta. Kauda kanta tayi sosai tana dauke numfashin da zuwa sannan tana jin kamar ya fara daina isarta "Ba wannan hijabin ba?" Ya fada yan yamutsa hijabin cikin hannunsa,abinda ya sanya ta takurewa gaba daya guri guda tana qoqarin neman hanyar da zata samu iska me kyau gudun gushewar hankalinta,wanda wannan na daya daga cikin damar da zai samu cikakkiya kan ya aikata komai hankalinsa kwance. Wata wawiyar zuqa ya yiwa wiwi din ya sake fesa mata kan fuska,sannan ta birkitota gaba daya yana kici kicin fincike hijabin daga jikin ta. Dole ta daga fuskarta,duk da yamutsewar hazon dakin dole ta bude kafofin shan iskarta ta fara masa magana a rarrabe "Kada ka ketamin haddi na,kada ka lalatamin mutuncina" Tayi.maganar sanda ya samu nasarar salube kan hijabin daga kanta. Bayyanar sassalkar sumarta ya sanyashi sake gigicewa,bai taba tunanin ta mallaki suma har haka ba. "Wow" Ya fada yana qoqarin samun wuyan hijabin don itace hanya mafi sauqi da zata bashi damar tsarge hijabin cikin sauqi daga jikinta. Ta fahimci abinda yake shirin yi,saita tattara dukka dan qarfinta ta cukuikuyeshi da kyau tana kiran sunansa cikin qaraji gami da fadin "Kada ka aikata!.....ka qyaleni mashkurrrr!!!!". A hankali ya bude idanunsa wadanda basu sauka akan komai ba sai agogon dake gefan gadon nashi. Idanu ya zuba mishi kafin ya miqa hannu a hankali yana jawoshi yana duba time da weather na gari. A nan yaga alamun saukar ruwan sama,sai ya maidashi sannan a hankali ya furta addu'a yayin saukar ruwan sama 'ALLAHUMMA SAYYIBAN NAFI'AN'. A nutse ya tashi daga kwanciyar,ya motsa kadan yana sauke qafafunsa daga qasan gadon wanda suka sauka daidai bedroom slippers dinsa yana jin yadda gaba daya ciwon kan da yakeji din ya sauka. A yanzun tsabar ta'ammali da home remedies ya sanya ba kasafai ya fiya afawa kansa qwayoyin bature ba yayin zazzabi da ciwon kai ba. Miqewa yayi ya fara takawa zuwa qofa yana mamakin yawan baccin da yayi,yadan shafi cikinsa yana jin yadda yunwa ta fara yamutsa hanjinsa,don haka ya yanke shawarar ya sauka qasa kawai yaci abinci,yadan duba ayyukansa koda na awa biyu ne kafin ya sake kwanciya. A parlor ya tsaya ya duba wayarsa,ya samu tarin miscal amma ciki na farouq yafi yawa,ya samu saqonsa da yake masa mita akan bai bada komai na tafiyarsu ba bayan saura sati guda. Qasan zuciyarsa kawai yayi murmushi yana sauka daga duba saqonnin. Har ya aje wayar wani tunani ya fado masa,sai ya tsaya ya zubawa qofa idanu. Yana tuna tahowarta ne jiya daga bedroom dinta zuwa qofan falo. Tabbas idan idanunsa ba qarya sukayi masa ba kallo yaga tanayi. "A ina ta samu waya?,waye ya bata waya?" Ya yiwa kansa tambayar a bayyane yana zurfafa nazarin ta inda zata samu waya tana cikin gida. Kaman yadda ya sanya doka ya sani ba wanda ke shiga gidan,sai amna da tazo baifi sau biyu ba. Amna kuwa yayi imanin ba zata taba bata waya ba musamman idan ta gaya mata shi ya karbe. Duk abinda yayi ko ya aikata amna tasan yana da dalili,ta fita saninsa,so ba zata karya dokarsa ba. Kai ya jinjina yana tuna fitar da tayi ba tare da sani ko izininsa ba rannan,tabbas wayar tana da alaqa da wannan fitar duk da ya bincika babu wani abu da yayi kama da gurin wani taje.....amma how and when ta samu waya?. Tambayar data masa susa kenan a qirji. Yanaji kaman ya kamata ya maida hankali a saka CCTV din. Company din yazo har sau biyu shi yace su bari ya zama free ya kirasu,yana jin kamar gamsuwa daya fara bawa kansa don tana karatun addini sosai a yanzu ta hannun jikar malam.....kaman bai kamata ya bata amanna har haka ba. Da wannan tunanin ya bude smart door dinsa,ya kuma fara sauka zuwa qasa. Abinda ya soma bashi mamaki shine jin gaurayar wani qamshi qamshi me kama da wari wari da gauraye stairs din. Koda ya kawo qarshenta sai yaji warin yana dada qarfi,ya tsaya cak yana buda hancinsa sosai,a nan yaji daga inda warin yafi qarfi. Mamaki ya kamashi sosai,yana da wani irin experience na iya hasashen abu da gano sauyawar motsi ko yanayi kaman wanda ya karanci aikin binciken tsaro na sirri. Fara takawa yayi zuwa cikin hallway din a hankali,yana sake shiga ciki xarginsa kuma na sake qarfafa saboda daduwar warin da sai a sannan ya fahimci warin wiwi ne. "Wiwi?" Ta maimaita sunanta can qasan maqoshinsa sanda ya iso bakin qofar dakin. Tsaiwar da yayi duka baifi ta minti guda ba,amma sai yaji jikinsa bai aminta da dakin ba,baya buqatar yayi knocking don ba qa'idar bincike bace akan abinda kakeson ganin gaskiyarsa quru quru,juyawa yayi da sassarfa yana tuna inda yaga an tanada a dakin nasa saboda ajiye kowanne key na kowacce qofa ta gidan a matsayinsa na mamallakin Master bedroom. Dubawa daya ya hango master key,sai ya daukoshi yana juyawa gami da saukowa kai tsaye yana nufar hallway din. Ta riqe ya riqr,yaja taja,har daga baya ya fahimci kamar hayaqin wiwin din kawai ke iya bugar da ita. Hakan ya sakashi tsugunnawa ya dauki guntuwar data rage,ya jata da kyau ya fesa mata a fuska. Numfashin ta ne ya soma yankewa,ta jawoshi da wani irin hanzari tana tuna komai zai iya faruwa idan ta sake ta rasa numfashinta. Ci gaba yayi da bulbula mata tana ci gaba da riqe numfashin nata da taimakon hasbunallahu wa ni'imal wakil da take ambata cikin maqogoronta. Dariyar mugunta ya saki,sai kuma yace "Are you asthmatic?" Bai jira komai ba ya danna mata wiwi din a baki,abinda ya birkitata kenan ya sanyata hautsinewar da batasan sanda ta daki al'aurarsa da gwiwar qafarta ba,tsananin zafi ya sakashi sakinta gami da hankadata....dukka jikinta ya gama saki,numfashinta kuma yayi qaura daga gangar jikinta,wannan ya sanyata tafiya luuuuu bakin qofar dakin,wanda haka dama ya saita da nufin fuskarta ta daki qofa ta kuma suma kafin ya gama daidaita radadin daya ziyarceshi. Saidai kuma tana isa bakin qofar sai yayi daidai da sanda ya murza handle ya bude,abubuwa biyu duka dakeshi,warin wiwi da fadowarta qirjinsa da guntun wiwin a bakinta,sulalewarta a jikinsa ya sanyata ta gangara ta fadi ta gefen bakinta,ta qarasa zubewa a jikinsa unconscious. *_DUNIYATA LITTAFIN KUDI NE(PAID BOOK),KAI TSAYE KI TUNTUBI WANNAN NUMBER_* 08187255862 𝐃 𝐔 𝐍 𝐈 𝐘 𝐀 𝐓 𝐀 _Zafafabiyar_ ̶B̶O̶O̶K ̶2 ⱧɄ₲Ʉ₥₳ 𝙋𝘼𝙂𝙀 58 58 _Daga ibn abbas RA,manzan Allah S A W yace"duk wanda yaji kiran sallah baije yayi sallar ba(ya zauna ya yita a gida).to bashi da sallah,saidai idan wani uzuri ya hanashi fita(kamar yanayin firgici na rashin tsaro ko tsoro)_ Dukkanin hannayensa ya sanya tallabota jikinsa yana bin guntun wiwin din daya fadi da kallo. Maido dubansa ya sakeyi fuskarta cikin wani irin yanayi dashi kansa baisan yadda zai fassarashi ba,sannan ya sake daga kansa yana bin mashkur dake tsaye da wani birkitaccen kallo. Na wucin gadi tsaf tunaninsa ya tsaya kafin qwaqwalwarsa ta dawo da aiki,yayi hanzarin maida dubansa fuskarta da take bayyanar da gushewar numfashi a tattare da ita. Tattarota yayi sosai sannan ya dagata cak yana jin wani abu yana zagayaw a gangar jikinsa. Waye wannan cikin dakinta?,waye wannan da yanayin da ya tabbatar masa ba mutumin kirki ko aziqi ne ba.....me ya kawo qaton gardi cikin tsakiyar dakinta daya kaure da mummunan warin wiwi. Duka yana da buqatar wadannan amsoshin,to amma kuma hankalinsa ya rabu gida biyu yana jin kamar ya fara cetar numfashinta da ya dauke shine abu mafi muhimmanci na farko a tare dashi. "Ina zakaje da ita?" Muryar mashkur dake a shaqe ta sauka a kunnuwansa sanda ya fara dosar qofar dakin da ita. Wani mahaukacin mamaki ya kasheshi daya sanyashi waiwayowa ya zubewa mashkur idanunsa. A karon farko kaifin birkitattun idanun fu'ad din suka ratsa nasa jijiyoyin idanun suka kuma aike saqo ga sassan jikinsa,saidai kuma a yadda yakejin zuciyar tasa a tsike......ba muhammad jadda ba...koma waye zai iya fito na fito dashi indai akan cikar muradinsa ne. "Shawara zan baka ka ajiyeta ka rufe mana qofa......don ba suma ba......ko mutuwa tayi tabbas sai na biya buqatata a kanta.......ita ta kira wannan ruwan.......ita ta kira fitina a sanda fitinar take bacci". Wani dummmm fu'ad yaji kunnuwansa sun masa na wani lokaci,take wani irin gumi ke dumi ya soma fesowa ta kowacce kafar gashi ta jikinsa. Idanunsa suka soma sauya launi tamkar an diga jan zabibi a cikinsu. Murna da mamaki suka cakude suka saukarwa mashkur sanda yaga ya sake turo qofar dakin yana dawowa. Saidai shakku sun cikashi a sanda yake tuna waye muhammad fu'ad?......wanne risk ya tsallake kafin ya zama abinda ya zama yanzu?,kafin ma ya mallaki asalin abinda ya zama shine silar arxiqinsa a yanxu?. Kyakkyawar ajiya yayi mata saman sofa din,da wani irin zafi ya miqe yana nufar inda mashkur yake tsaye yana danne da inda ta doka masa bedside lamp da har yanzu wajen yake masa matuqar zugi. Tun daga yadda idanunsa suka jirkice da kuma yadda jikinsa yake wani irin shaking hankalin mashkur ya fara dawowa jikinsa. "Dakata!......kada ka qaraso nan wajen!" Mashkur ya fara da qarfi shima yana qoqarin ciro bindigar dake maqale a qugunsa. "Waye kai?!" Fu'ad ya watsawa mashkur tambaya da sautin tsawar data sanya dukka dakin ya dauki amsa kuwa ba tare daya damu da bindigar dake riqe a hannun mashkur din ba. "Sanin koni wanene bazai maka amfani ba......abu daya zan baka shawara kaman dai dazu,ka juya ka fita salin alin ka barni da ita". Kalmar tasa ta qarshe ta sake zamantowa tamkar digar ruwan dalma saman sabuwar fatar jariri. Ya daga qafarsa ya soma takawa da wani irin fushi zuwa inda mashkur ke tsaye idanunsa na sake ninka rinewarsu,kai kace bai fahimci da gaske bindiga bace a hannun mashkur ba. "Waye kai!!!" Ya sake maimaitawa kaman zai tsaga dakin da muryarsa yana jin wani bala'i daga saman zuciyarsa. Takowar tasa da yadda yake durfafarsa ba wani sauran tsoro......yana tunkararsa ne kai tsaye kaman bindigar wasan yara ce riqe a hannunsa bata gaske ba shine yake saka dulmiya mashkur a matsanancin mamaki......mamakin da yake qarasa dauke ragowar duk wata nutsuwa dake jikinsa yana kuma dagula masa lissafi da Kalar jarumtar da yake hange tattare dashi. "Ina sake gaya maka,kaman yadda ta jawoni rayuwarta......yau ko zaka mutu sai na kwanta da matark......." Bai samu daman qarasawa ba saboda saukr kwalbar turare saman daidai bakinsa,ta kuma fashe a take,abinda ya bata daman yankan wani sashe na fuskarsa.......ya kuma sanya jini soma diga. Saukar kwalbar a fuskarsa ya sanya bindigar subucewa daga hannunsa. Jinin daya soma diga a fuskarsa baija hankalinsa ba fiye da faduwar bindigar daga hannunsa. Yayi imani bashi da garkuwar data wuce masa bindigar,kuma muddin ta subuce masa to tabbas dukkan wata dama ta subuce masa,tuna wannan ya sanyashi durqusawa ya saka hannu yana laluben inda ta tsalle ta fadi. Daga can gefan gadon ya hangota,da azama da kuma sassarfa ya zura hannunsa da zummar daukota,saidai kuma ya makara,don yana dora hannunsa akai qafar fu'ad na sauka saman hannun nasa. Da dukkan qarfinsa ya take masa hannun,wani irin zafi da radadi suka ziyarceshi yana jin kamar dukka yatsunsa biyar sun karye. Daya hannun nasa mashkur ya sanya da nufin ture qafar fu'ad din,amma ta nan ma ya rigashi ta hanyar sanya daga qafar tasa ya daki tsintsiyar hannun fu'ad din,bai kuma bari radadin ya gama ratsashi ba ya sake take daya hannun da dole ta sakashi ya zare hannun daga saman bindigar. Da qafa fu'ad ya daki bindigar ta qarasa shigewa can qarqashin gadon,abinda ya daga hankalin mashkur kenan "Komai zai iya kwabemin......dole na samu abinda nazo nema koda guda daya ne cikin biyu...." Bai qarasa qulla mafitar data dace dashi ba wani kyakkyawan naushi ya saukar masa a tsakiyar kansa. Azaba ce ta ratsashi tun daga tsakiyar qwaqwalwarsa har zuwa tafin qafarsa,bai murmure ba wani lafiyayyen naushin ya sauka a kumatunsa. Qarfin naushin ya sakashi yin baya,yayu taga taga zai fadi ya dire da qafarsa. Cikin abinda bai gaza second daya ba yaji wani abu me yauqi da gishiri ya cika masa baki,dole ya hadiye ko ya zubar wanda zubarwar yakejin zaifi masa,sai ya furzar din yana jin yadda kansa ya sake qullewa da azabar data zarce har cikin bakinsa. Furzar da jinin saman marbles din ya bada sauti,saiga haqoransa nan jere reras guda hudu da haskensu ya bayyana cikin jajur din jinin. Idanu warwaje yake duban fu'ad,ya tabbatar ya masa illa ta farko kenan da har ya mutu da ita xai tafi lahira?,zuciya ta ciyosa,ta yaya yana namiji shima haka ya tsaya ya masa irin wannan barnar,wannan tunanin ya sanya koda yakai masa naushi na uku ya kauce ya naushi iska,sannan kuma hannunsa ya zarce zuwa ga glass din madubi dake daura da wajen,take ya tarwatse zuwa piece's,ya kuma samu lallausar fatar hannunsa ya yanki inda yakeso. Cikin qasa da second daya shima jini ya soma diga da mugun gudu a a tafin hannunsa da bayan hannun nasa,wannan shine abinda ya baiwa.mashkur qwarin gwiwa,ya kuma Tunxura fu'ad ya sake kai masa wani naushin ba tare daya damu da jinin da yake zubarwa ba. Ya sake samunsa still a wuyansa,zuwa sannan qaramin fitsari ya qwace ma mashkur saboda azabar da yaji ta sauka akan kowacce jijiya tashi. Yanke hukuncin maida martani yayi,cikin nasa fushin yakai masa nasa naushin yans cewa "Bari na nuna maka iya tawa bajintar" Saidai baiko qaraso inda yake ba ya yiwa hannun nasa wani mummunan bugun da sai da yaji qarar qaramin qashin dake riqe da tsintsiyar hannun nasa. Wani ihu ya kwarara don azaba,ihun da lallai inda qaramin gida ne wala'alla har jama'ar dake farkon layinsu sai sunji......sautin ihun nasa ya samu ratsawa tsawa ta kowacce kafa dake dakin,ta kuma isa ga kunnen daya daga cikin securities na gidan dake on duty a daren,yaketa kuma kai kawo domin tabbatar da tsaron gidan da amincin masu gidan. Tsayawa yayi sosai yana son tantance daga inda qarar ya fito,a lokacin fu'ad ya sake isa inda yake ya kuma daki gwiwarsa da qafa,abinda ya sanyashi zubewa saman gwiwoyin nasa shima yana sakin ihu karo na biyu saboda yadda yaji qoqon gwiwarsa kaman ya fice fit daga jikinsa. "Zan saka kayi nadama,zakayi dana sanin abinda kakemin......wallahi sai na d'an d'ani xumarta kamar yadda kuma kuka d'an d'ana......saina huce fushina a kanta,sai nayi mata fata fata......" Wani mulmulallen abu me kama da wuta yazo ya daki zuciyarsa,har baisan sanda ya sake saka hannu yakai masa dukan daya sanya haqoransa na gaba wannan karon suka baqunci waje ba yana wani irin huci kamar tsohon kumurci. A gigice ya sake fidda idanunsa yana kallon haqoransa guda biyar zube a gabansa cikin jini,a qiyasi ya rasa haqora aqalla goma sha biyar,sha biyar suka rage masa a baki......sai ya saki wata kururuwar data tabbatarwa security din daga cikin gidanne. Wayarsa ya zaro ya fara kiran number gaggawa ta cikin gidan,saidai kiran daga parlor hallway xuwa sassansa ya tsaya,bai kawo dakin sabreen ba saboda datse layin da mashkur yayi. Cikin gunji duk da yadda jini yake ambaliya a bakinsa amma bai fasa duban fu'ad dake jawo wata cable me kauri ba yace "Saina lalata rayuwarka......sain......" Maganan ta katse saboda wani naushin daya sake xuba masa a tsakiyar kai,take wuta ta dauke masa,sashen maganarsa kuma ya dakata na wucin gadi,sannan ya tafi yifff ya fada akan jininsa jikinsa yana saki,komai baya aiki illa numfashinsa dake fita a wahalce. Da qafa ya dakeshi ya juyashi,ya tsugunna yana sanya cable din daga hannunsa zuwa qafafunsa,sai daya tabbatar ya daureshi sosai sannan ya fara jansa kaman mushe ko kayan wanki yana bude dakin ya fiddoshi. Sai daya kawo parlor na biyu sannan ya zubeshi a tsakiya. Jijiyar kansa na wani mugun gudu da harbawa ya qarasa gaban telephone ya fara kiran sashen tsaro na gidan. "Yes sir......" Security din dake tsaye yana jiran kota kwana ya fada sanda kiran fu'ad ya riskeshi. "Ku bincika min cikin gidan nan da kewayensa.......ina kyautata zaton akwai wani mutumin daban.....na baku minti goma kacal" Yadda yaji muryar boss din nasu a yau sai yaji wani tsoro da razani ya kamashi,bai taba magana dasu da irin wannan sautin dake cike da fushi da tsawa ba. Maida wayar yayi sannan ya matsa cikin hikima ya qyasawa abokin aikinsa. A zuciye ya wurgar da kan wayar,sannan ya juyo yana takowa zuwa inda ya ajiye mashkur. Zagayashi yayi har kusan sau uku,zuciyarsa na masa wani irin tsalle a qirji,ba abinda zuciyarsa ke gaya masa illa ya dauko bindigar ya fasa tsakiyar kansa da ita. Numfashi yaja sosai,sai ya juya yana komawa ciki bayan tunawa da yayi da ita,sa'annan muddin yaci gaba da zama a gaban mashkur zai harbeshi dinne abinda yaketa qoqarin hana kansa aiwatarwa. A bude qofar dakin yake,wannan ya bashi damar shiga kansa tsaye. Dakin da zuwa sannan gaba daya komai na cikinsa ya hargitse,banda fasasssun glass da kwalaben fitilar data kwatsawa mashkur ba komai a qasan,sai wargatsatstsun kayan dake saman dressing table dinta da suka tarwatse a qasa. Inda take kwace ya maida idanunsa,har yanzu tana kwance inda ya barta din,idanunsa kafe a kanta ya qarasa gabanta. Sauka idanunsa yayi a saitin bakinta,pink lips dinta da suka sauya launi kadan suka kuma bushe qamas,hoton yadda wiwin ta zauna akan lips dinta ya dawo masa,wani mulmulallen abu ya tokare masa wuya,da sauri ya ture hoton daga kwanyarsa,ya tsugunna a gabanta yana tunanin me zaiyi mata?,me ya kamata ya fara yi?. Sake maida dubansa yayi ga fuskarta wadda har dogon dokin wuyanta ya bayyana,hakanan wani sashe na kafadunta saboda saukar hijabin da ya fara samun nasarar yagawa. Sauka dubansa ya qarayi xuwa saitin qirjinta,inda a daidai nan hijabin ya nuna muguwat cukuikuyewar da zata gaya maka an riqe wajen ne da mugun riqo. Qirjinsa yaji ya wani doka,yawun bakinsa kuma yaji ya dauke qaf kaman ba'a taba halittar yawu cikin bakinsa ba. Abinda bai taba ji ba tsahon rayuwarsa yau karon farko ya jishi......wata mummunar faduwa gaba,sannan take yaji hannuwansa da qafafunsa sun fara rawa sakamakon tunanin daya bijiro masa. Sake xubawa wajen ido yayi,yayin da zuciya ta fara masa imagination na hannuwan mashkur a wajen,wani abu me qarfi ya daki zuciyarsa har sai da ya fusgo numfashinsa da kyau,dai dai sanda yaji itama ta ja numfashin da matsanancin qarfi har sai da qirjinta ya daga. *_DUNIYATA LITTAFIN KUDI NE(PAID BOOK),KAI TSAYE KI TUNTUBI WANNAN NUMBER_* 08187255862 𝐃 𝐔 𝐍 𝐈 𝐘 𝐀 𝐓 𝐀 _Zafafabiyar_ ̶B̶O̶O̶K ̶2 ⱧɄ₲Ʉ₥₳ 𝙋𝘼𝙂𝙀 59 59 Da wani irin yanayi numfashin nata ya soma fita,abinda ya sanyashi karon farko tunaninsa yazo masa cewa asthmatic ce. Miqewa yayi yana ranqwafawa saman kanta da nufin dagota ya canza mata makwanci duk da abinda yakeji,yana dagata din towel din jikinta yana zamewa ya kuma fadi saman qafafunsa. "La haula wala quwwata illa billah" Ya furta a sarari da wani irin bugawa da zuciyarsa tayi yana jin sautin har cikin kunnuwansa. Wani jiri da dan qaramin duhu yaji yana mamayarsa har sai daya lumshe idanunsa yana jan numfashi da kyau,ya tattaro dukka ragowar qarfinsa ya hada waje daya sannan ya soma takawa da ita ya ajiyeta saman gadon. Zamewa hijabinta ya qarayi,santala santalan fararen cinyoyinta suka fito,ya dauke idonsa da sauri yana jin yadda bugun zuciyarsa ya dake qaruwa,sai ya sanya hannu yana jan hijab din yana jin zuciyarsa na qara quntata waje daya kaman an daureta a tsakanin qirjinsa "Why?" Ya fada da mabayyanin sauti yana jin idanunsa na masa wani yaji yaji. Ta yaya wani zai samu hanyan shigo masa gida?,garin yaya hakan zata faru?. Kai ya girgiza,hankalinsa bazai dauki wannan ba.......kanshi da tunaninsa ba zasu iya karba ba. Taimakon gaggawa ya soma bata kaman yadda sukewa anni idan irin haka ta taso. Sam ya kasa hada bakinsa da nata saboda warin wiwin da yake tashi daga ciki,wanda yana daya daga cikin abubuwan mayen da ya yiwa muguwar tsana. Laluba aljihunsa yayi,sai a sannan ya tuna da wayarsa,ya cirota a nutse yana budewa gami da nemo number saddiq. Saddiq dinne kadai yasan bai fiya bacci da wuri ba,shima kaman shi yake,yanayin aikinsu ya sanya sukan iya raba dare a gida suna rage ayyuka. Bugu daya tak kuwa ya daga,muryarsa can qasa yace "Barka da dare hamma..." Bai amsa gaisuwar tasa ba yace masa. "Ka nemomin Dr rubayya......please ku kawota gida yanzu if possible" "Subhanallah...waye baida lafiya hamma?". Rasa amsar ma da zai bawa saddiq din yayi,sai kawai yace masa "Ba wani abu bane can.....just kayi sauri ku qaraso". Sauke wayar saddiq yayi yana duban farouq dake zaune a gefansa,wanda tunda ya daga wayar yaji da waye suke waya ya maida hankalinsa wajen duk da idanunsa suna kan system dinsa yau din yana sashen su saddiq dinne,don shima aiki gareshi sosai,sun samu sabon iri da sukeson su fara gwadawa manoma da manyan manoma da 'yan kasuwa,yanaso yayi settling na komai kafin ya kwanta,charger dinsa na system dinsa tayi masa tutsu,dole ya shigo ya karbi ta saddiq din ya jona gudun kada tayi shutting down. "Lafiya yace maka ba?" Farouq ya fada kansa tsaye yana duban saddiq. Daga masa kai saddiq din yayi,sai farouq din ya soma tattare ayyukan nasa waje daya ya killace yana cewa "Ka kirata kace zamu biyo mu dauketa......fu'ad bazai taba gaya maka worsening na komai ba indai shine". Ya furta yana saving ayyukan da sauri cikin aikin nasa,wannan ya sanya saddiq shima ya soma qoqarin kiran nata. Sai daya ajiye wayar saman bedsheets dinnan sannan ya lura da hannunsa da har yanzu yake tsatsafar jini. Radadin dake cikin zuciyarsa ya danne wanda yake ji a hannunsa,shi yasa sam bayajin komai a hannun nasa. Idanunsa ya sake mayarwa kanta,sai kawai ya samu kansa da miqewa yana daukan wayarsa,ya daidaita iskar dakin saboda gumi daya gani saman goshinta ya qara hasken qwan dakin sannan ya fara takawa cikin takatsatsan gudun kada ya taka wani abu ya soma fita a dakin yana komawa parlor. Tun bai qarasa ba ya hangesu sun cika hannunsu da wani baqin kakkauran matashi wanda ke sanye da baqaqen kaya full dress,tun daga hula riga zuwa wandon jikinsa. Iya riqon da sukayi masa kadai zai gaya maka yadda ya matsu a hannunsu. Ci gaba yayi da takowa yana karantarsa,duk wani alamu dake nuna tashin hankali da rudani sun tabbata a fuska da jikinsa. "Sakeshi" Fu'ad ya fadi yana jin hatta da security din gidan suma a yau bazasu tsira a hannunsa ba. Gaban mashkur ya qarasa ya zauna saman kujerar falon "Ku zaunarmin dashi a nan" Ya fada yana musu nuni da gefan mashkur din. Wani mugun duka sukayi masa wanda ya sanyashi zubewa ba shiri yana fasa qara. "Ku jirani a waje" Fu'ad din ya fadi yana qoqarin hana jinin dake diga a hannunsa bata sofa din da yake kai. Kallon fu'ad kawai matashin yakeyi,yana jin yadda kashi da fitsari gaba daya suke neman kufce masa,saidai kuma yasan babban kuskure na gaba da zaiyi shine ya saki fitsari ko kashi a wannan kyakkyawan falon. Zai iya cewa a tarihin rayuwarsa kaf.....a tarihin manya manyan laifukan daya aikata a rayuwarsa bai taba cin karo da mutumin da yayi masa kwarjini irin muhammad jadda ba. Yana zube a gabansa yana jira yaji koda wata kalma daya daga bakinsa amma ko qwayar idanunsa bai daga ya kalleshi ba bare ya sanya ran wata tambaya zata biyo baya,ta goge jinin hannunsa kawai yake da lallausar tissue din daya ciro a tissue box din dake gefansa. Bawai yayi hakan bane saboda ciwon yana da muhimmanci a rayuwarsa ba.....a'ah......yayi shuru ne saboda a yanzu babban muradinsa shine yayi mummunan lahani a garesu da babu me iya gane fuskokinsu,duk kuwa da cewa ko a yanzun fuskar mashkur ta haye tayi kumburin da dukka wata halittar fuskar ta sauya daga asalin yadda take,abinda yake sake sanya tsoro me yawa kenan ga zuciyar hanzari. "Don Allah me gida.... Kayimin rai,ka tausayamin me gida......don girman Allah". Kalaman hanzari kenan wanda ya gaza jiran yaji abinda fu'ad din zai fada. Cillar da tissue din yayi,sannan ya daga idanunsa da har yau launinsu bai koma daidai ba ya aza akan hanzari "Waye ya gayyato ka?,duka ku biyun kuma waye ya aiko ku?' Tambayoyi guda biyun da a wajen hanzari suke masa kamanceceniya da tambayar kabari ga kafiri a ranar daren farko "Shine!.....shine wallahi" Hanzari ya fada yana nuna mashkur dake yashe a qasa har yanzu bakinsa na fidda jini. A yadda mashkur din yake yayita qoqarin murgina kai ya kalli koda idanun hanzari ne amma ya kasa ballantana ya fadi wata kalma da zata zama kariyar kai a gareshi. Kiran sunan mashkur da hanzari yayi shine abu mafi sauqi.....mafita mafi sauqi a gareshi akan ya ayyana ko ya ambaci daga inda ainihin kwangilar aikin ta fito,wanda fadin daidai yake da fadawar mutanen da suka jibanceshi da yawa cikin masifa da bala'in da baisan ranar fitarsu ba......gwara ya danganta kanshi da mashkur.....kusan yasan waye.....kuma koda yafi haka hatsari yazan bazai zartashi a hatsari da hatsabibanci ba.......koda ya zartashi yasan bazaikai mutanen da suka qirqirar da aikin ba. "Kana da masaniyar cewa maqabarta ka kawo kanka?......nan da kake zaune Motuare ce?!" Ya furta da sautin da hatta da mashkur sai da yaji kaman an buga masa guduma still saman ka bayan masifar azabar da yake ciki. Firfito da idanu hanzari yayi.......yayi gwagwarmayar rayuwa da yawa......ayyukan rashin imani bila'adadin......ya shiga komar Jami'an tsaro masu yawan gaske......da wannan kadai yana iya gane mutum da muhallin da ake magana ta gaske kai. Salati ya debo wanda ya manta rabon da ya ambaceshi a bakinsa,sallah kanta ba'a maganarta sam bars aje ga gurbin xama ayi wani xakiri ko tasbihi. "Zip your mouth!" Fu'ad ya furta da fushi "Ko burbushinku ba zaa samu ba.......daga yau ba zaku sake gigin tsallaka gonar wani ba" "Innalillahi wa inna alaihi....." Ya jiyo muryar daga can gefe tana fada cikin maqyarqyata saboda tsananin tsoron data shiga. Duk tsawarsa guda daya sai taji kamar ana finco mata hantarta tare da qoqarin bintiko zuciyarta daga muhallin da take a dashe. Waiwayawa yayi yana mamakin wanda ya rage a falon bayan ya bada umarnin kowa ya fice. Zuwaira ce tsaye yana rawar dari kamar wadda ruwan da yayi saura har yanzu yake sauka kadan kadan a kanta ya qare. Sulalewa tayi a wajen tana jin wata razana tana saukar mata,idanunsa sun mata wani kaifi da bata da juriyar daukarsu. Yadda yake magana ga duk wanda yake falon zai tabbatar abinda yake fadin zai aikata ne. Ba wasa ko digo cikin kalamansa. Itakam a yanzun ina ta shirya mutuwa?,a irin wannan qadamin da take lissafin sake inganta rayuwarta da jin dadin da yake hange daga wasu?,itama ta samu ta dandala ta baza nata ikon da isar kafin zuwan randa zata bar numfashi?,shine tun a yanzu a gabanta wannan manya manyan alkaba'in yake faruwa?. Idanu ya zuba mata da kyau yana qoqarin karantarta,saidai kuma kafin yayi nisa an murza pivot door din daga can wajen falon an shigo. Farouq ne a gaba,Dr rubayya a tsakiya sai saddiq daga bayanta . Shigowarsun kawai cikin falon....hada idanunsa da farouq sai yaji kaman an janye wani kaso na bala'i da masifar da yakeji tana kunnuwa cikin zuciyarsa. Wani irin tashin hankalin da baisan dame zai fasaltashi ba. Dr rubayya na qoqarin gaidashi.....saidai shi hanyar hallway din kawai yake nuna mata da yatsa ba tare da yace komai ba,sai itama bata sake magana ba kasancewar halinsa ba baqonta bane,ta wuce da kayan aikinta kai tsaye zuwa hanyar. "Ka leqa ka kiramin saddam......suzo.su biyu" Yace da saddiq da rinannun idanunsa da suka sanya saddiq shan jinin jikinsa bayan mutane biyun da ya gani zube a wajen. Shima baice komai ba ya juya yana fita daga falon. A nutse farouq ya isa gabanshi,ba tare da yace komai ba duk da idanunsa na nuna kaduwa da abinda yake gani ya kama hannunsa yadan juya sannan ya saki "Dude.......wai meke faruwa?" Ya qarasa maganar yana saka idanunsa cikin na fu'ad din. Janye nasa idon faud din yayi daga na Farooq yana hadiye wani abu me tauri daga qasan zuciyarsa. To shi ta yaya ma zai fara bada wannan mummunan labarin?,yace meye?,yace masa wiwi ya kamasu suna sha har ya bugu asthma dinta ya tashi?,ko yace masa ta gayyato maza cikin gidan sun bugu sukaso gwada mata qarfi?,ko kuma yace sharri akayi mata?,barayi zai kirasu ko 'yan fashi?,zaice sun hauro masa gida ne?,gida ma irin nasa?,gidan da ba wani abu daya isa ya shiga ko ya fita cikinsa saida cikakken tsaro da kulawar security......waye hankalinsa zai dauka?,waye zai yadda da wannan labarin?. "Ka kwashesu ka sakaminsu a cage din dogs dincan....." Ya fada yana miqewa sanda hanzari ke qoqarin riqo rigarsa a gigice "Kayi mana rai oga.....ka hukuntamu duk yadda kaso,amma kada ka hadamu da karnukan can.....wallahi ko kafin safiya sun gama cinye namanmu oga...." Yayi magana fitsarin da yaketa son riqeshi yana kubce masa. Tun shigowarsu gidan yanayin karnukan ya tabbatar masa sunsha banban da dukka karnuka daya sani. Basu bi ta gefensu ba.....amma wani abun mamaki yadda suketa haushi ya ninku,yana ganin sanda me kula dasu ya dubasu,ya kuma yiwa security na gidan magana suna sake bincike sassannin gidan amma basu ga komai ba saboda sun shigo ne ta hanya mafi sirri da samun tabbaci,kuma sun samu mafakar da binciken me bincike bazai taba kaiwa nan ba. "What are you waiting for?!!!" Fu'ad da dama dukkaninsu suma a cike yake dasu ya fada a tsawace,ba shiri suka durfafesu,hanzari yayi wuf ya kama qafarsa yana sake roqonsa. Wani wawan duka yakai masa da qafar daya sanya hanzari zubewa warwas,basu saurara masa ba suka sungumeshi suka hada da mashkur da tsabar razana ya kasa magana,sai yakejin kamar qiyama ce zata tashi. Yasan illar karnukan,don sanda yake sharafinsa ya ajesu a gidansa sun kusa guda biyar,hakanan baisan adadin mutanen da ya sanya suka yagalgala ba. "Karku sakasu a cikin cage din.....ku ajiyesu dakin kusa dashi" Ya basu umarni sanda suke kicin kicin fita dashi. "Okay sir" Suka amsa masa sanin wayeye farouq wajen boss din nasu. Shi daya ne duk duniya yake tada hukuncin da fu'ad yayi kuma ta zauna ba tare da haufi ko kankare ba,shi yasa suka karba umarnin nasa kaman yadda ya basu. Yadda yaga komai yasan ba lafiya ba.......yadda kuma yaga yanayin hannunsa da gidan ya tabbatar akwai gagarumin wani abu daya faru.....uwa uba wani kwantaccen fushi d yake gani a fuskar Fu'ad ya sanar masa akwai matsala ko a yadda ya fita a fusace. *_DUNIYATA LITTAFIN KUDI NE(PAID BOOK),KAI TSAYE KI TUNTUBI WANNAN NUMBER_* 08187255862 𝐃 𝐔 𝐍 𝐈 𝐘 𝐀 𝐓 𝐀 _Zafafabiyar_ ̶B̶O̶O̶K ̶2 ⱧɄ₲Ʉ₥₳ 𝙋𝘼𝙂𝙀 60 60 Tun bai qarasa inda yake hangen security na gidan daya tara ba yakejin muryarsa dauke da fushi me nauyi. Fada yake da duka zuciyarsa da jikinsa ma,sam kaman ya manta dare ne a yanzun......daren ma kuma irin daren da akayi ruwan sama ya dauke wanda ke ninka kowanne dare a shuru da daukewar sawu. "Your services are no longer required......you were fired!" "Ya salam" Farouq ya fadi,abinda yaketa sauri ya dakatar dashi kenan. Fushinsa na yau yanata bashi mamaki,sau tari shike daukan abu da sauqi......yawancin lokuta shike jan qafa da jan lokaci akan abubuwa irin wadannan......yana bin komai da lura a kuma tsare,har sai ya tabbatar dashi a inda ya dace. Kasa cewa komai yayi,don su kansu ma'aikatan da security din dake on duty a daren kowa cikin matuqar tashin hankali yake. Yadda suke roqonsa da mabanbantan harsunansu dukka sai suka bawa farouq din tausayi. Kowanne a cikinsu idan ka dubi fuskarsa ya kadu da hukuncin ba zata na me gidan nasu. "Calm down.....ya isa" Farouq ya isa gabansu yana fadi bayan komawar fu'ad din ciki. Hankulansu kuwa suka bashi cikin mutuwar jiki hankali a tashe. "Ku kwantar da hankalinku.....kowa ya koma bakin aikinsa kafin wayewar gari......but,ku sake tsaurara kula kafin muga abinda hali zaiyi. Duk da bawai tabbaci ya basu na cewa ya dawo dasu bakin aiki ba amma hakan ya faranta musu. Sun sani babu wani guri da zasu samu walwalar rayuwa da 'yanci da albashi me tsananin azabar tsoka kaman gidan jadda.....salary yake musu na kece raini......irin salary din da sunyi imani ko a villa suke aiki babu me biyansu irinsa. Uwa uba ga ihsani da alkhairi da suke samu kowanne lokaci,wanda ya kusan kamo abinda ake biyansu albashin aikinsu. Da yawansu suna jin idan ba gidan Muhammad jadda ba babu a inda zasu iya aiki,shi yasa suke riqe da aikinsu fiye da yadda ma yake tsammanin zasuyi. A parlor ya sameshi a tsaye kaman wanda zama ya gagareshi. Baice masa komai ba ya taka inda yake tsayen ya riqe hannunsa sannan ya wuce dashi,suka ratsa hallway din suka saura samansa. Saman monotti sofa ya zaunar dashi,ya taka da kansa zuwa shiyyar da aka tanada don ajjiye first aid box,don kusan yasan komai na gidan tunda shine ma tsara yadda zai kasance din. A gabansa ya zauna,ya bude box din ya ciro cotton wool da spirit ya tsiyaya ya fara goge masa ciwon. Sai a yanzu yake danjin radadin da hannun ke masa amma kadan kadan,saidai har yanzu abinda yakeji a zuciyarsa ya dara wanda ke a hannunsa. "Ko meye da sauqi ake daukarsa......da irin wannan temper din da kake ji a ranka komai fa bazai warware ba" Farouq ya fada yana qarasa goge masan,har yanzu kuma yana mamakin abinda ya birkita nutsatsen mutum irin fu'ad din. Duk da ya sani,ba abu bane me sauqi a keta alfarmar gidanka a shigo maka ba......to amma kuma yadda yasan fu'ad zai iya cewa tun wani zamani can daya shude rabon da yaga wannan attitude din a tattare dashi. Wayar tafi da gidanka din dake falon,wadda ke ajiye kusa da console mirror din parlor din ce ta dauki tsuwwa. Saddiq dake zaune daga gefe dukka jikinsa a mace ne ya dauka "Daga hallway bedroom ne" "Ka daga ko Dr rubayya ce" Farouq ya fadi sanda yake tattare ragowa ragowan audugan da yayi amfani dashi. Maganan second goma sukayi kwata kwata,ya sauke wayar yana duban farouq "Dr ce ke magana.....tace ta kammala......amma wai tanason ganin hamma". "Ka gaya mata tayi abinda ya dace kawai basai nazo ba" Ya fada yana jin ciwon kan daya tashi da jin dadin ya sauka yana son dawowa. Kai farouq ya girgiza yana dubansa,muryarsa a qasa qasa yadda saddiq bazaijishi ba yace "Dole kaje tunda tace kaje din.....dole saika gwadawa duniya halinka?" Idanunsa da har yanzu basu koma fararensu ba ya watsawa farouq,kaman zai magana sai kuma ya fasa ya tsuke bakinsa. Kamar bazai tashi ba kafin ya miqe yana kiran sunan Allah,wanda motsawar bakinsa ne kadai zaisa gane hakan. A hankali yake sauka zuwa qasan,saidai duk sanda ya kusanci dakin sai abun daya faru mintunan baya yayita dawo masa. Bama irin idan ya tuna ba komai a jikinta......daga ita sai towel sai hijab,sai yaji tamkar iskar da yake shaqa tayi masa kadan. Su biyu a daki tana daga ita sai shi.....su biyu a dakin da babu cikakkiyar sutura a jikinta......gaban hijabinta yasha cukuikuiya?.....duk sanda ya kawo nan sai ya lumshe idonsa saboda ji yake kaman an dauka adda an kafta masa sara a tsakiyar kansa. Handle din ya murza ya tura ya shiga da sallama saman labbansa. Ma'u dake gyara dakin ta dago daga kwashe sharar data gama,ta rusuna tana gaidashi duk da dare ne,sannan ta kwashe dustpan da vacuum cleaner din tayi waje dasu. Haka kawai ya samu kansa da bayason kallon fuskarta,don ba abinda yake tuna masa sai a yanayin data fado jikinsa. "Numfashinta ya koma normal,kuma yanzun haka bacci take me kyau.....ko da wanne lokaci ma zata farka abinta........amma please sir......koda asthma dinta baiyi tsanani ba at least ya kamata ace an ajjiye mata in healer.....and ya kamata ta dinga kula da gujewa ta'ammali da abubuwa masu hayaqi da yawa". Kai kawai ya jinjina ma Dr rubayya "Allah ya qara afuwa yasa kaffara.......idan kuma ana buqatar wani abun.....am ready in sha Allah,koda yaushe kuka kirani am available for your needs". "Thank you" Ya fada can qasa da kalar miskilancin nan nasa da ba wani baqon abu bane a wajenta. Already kafin ta fita ya kira saddiq ya gaya masa gata nan su maidata gida,yana kuma sauke wayar kiran farouq ya shigo masa "Mu duka mun wuce gida,but.....na kira wasu daga cikin guards dinka an qara akan na cikin gidan......in sha Allah kome zaiyi daidai......but please please.....karka dauki doka a hannunka akan mutanen nan". Farouq ya fada cikin narke murya. Ya dade da sanin halinsa,muddin ranshi yakai qololuwar baci irin wannan bai iya hukunci ba. "Kaji?" Farouq ya sake maimaitawa jin yayi shuru baice komai ba. "Alright" Ya fadi a hankali kamar wanda maqoronsa ke masa ciwo yana gintse kiran. Iska ya sake furzarwa daga bakinsa,daga jikinsa har zuciyarsa babu wani abu dake masa dadi,sai ciwo kawai.....wani irin ciwo me radadi a gangar jiki da zuciyar. Karon farko ya maida dubansa saman fuskarta,wanda daidai nan idanunsa suka hangar masa wayar dake gefan pillow dinta. Wani abu ya tsarga masa har yatsun qafarsa,sai ya miqa hannu ya dauko wayar. Tabbas itace wayar daya gani a hannunta shekaran jiya.....wayar da baisan yadda akayi taxo gidan ba ta kuma zama mallakinta har take amfani da ita. Jujjuya wayar yayi sosai yana qare mata kallo,sai ya latsa malatsin gefe haske ya kawo,ya sanya dan yatsa ya shafi fuskarta take ta bude. Bangaren kira ya shiga ya soma dubawa,kirane da numbers barkatai wanda kusan dukansu babu suna. Ci gaba yayi da dubawa har zuwa kan date din shekaran jiya wanda wata number data qare da 01 itace number qarshe da aka amsa kira da ita. Kai ya jinjina a hankali yana komawa bangaren saqonnin karta kwana wato sms. Dunqule hannunsa yayi da kyau yana ci gaba da duba saqonnin da suka shigo da mabanbantan numbers suma,wanda dukkaninsu suna dauke ne da nau'ikan kalaman soyayya iri iri,saidai kowanne saqo ba wata amsa guda daya da ta maida masa. Kasa ci gaba yayi da dubawa saboda yadda dukka jikinsa ya dauki tsuma,sai ya kashe wayar ya jefata aljihunsa sannan ya miqe yana dubanta da wani zafin zuciya. Takawa ya soma yi a hankali,har cikin jiki da zuciyarsa yana jin bazai iya zama da ita na daren gaba daya ba a daki daya,sai daya hau saman sannan ya kira sashen ma'u yace taje ta kula da ita,baima aje wayar daidai ba ya dora kansa a hankali saman sofa din yana fidda numfashi kansa kaman zai fado. Tunani ne iri daban daban suke barazanar tarwatsa masa kai,ya rasa da wanne zaiji?,da wanne zai fara?,meye daidai cikin hasashensa meye ba daidai ba?,ganin yana neman rasa nutsuwarsa cikin qasa da minti talatin,sai ya miqe a gaggauce ya jawo earpiece ya toshe kunnuwansa da karatun qur'ani,abinda ya sanya duk abinda yakeji ya soma sauka a hankali,nutsuwarsa ta soma daidaita,nauyin da yakeji a qirjinsa da zuciyarsa suka soma raguwa,sannu a hankali ya maida idanunsa ya lumshe wani bacci yana yin awon gaba dashi a cikin falon. *_TO ASUBA TA GARI......SAIDAI KUMA KO DAME SAFIYAR RANAR ZATA WAYE MUSU DASHI?_* *_DUNIYATA LITTAFIN KUDI NE(PAID BOOK),KAI TSAYE KI TUNTUBI WANNAN NUMBER_* 08187255862 𝐃 𝐔 𝐍 𝐈 𝐘 𝐀 𝐓 𝐀 _Zafafabiyar_ ̶B̶O̶O̶K ̶2 ⱧɄ₲Ʉ₥₳ 𝙋𝘼𝙂𝙀 61 61 Tun daga sanda ta farka bata samu wata nutsuwa ko kwanciyar hankali ba sai bayan data tabbatar ba wani abu a jikinta da mshkur din ya samu kaiwa gareshi "Allah na gode maka.....Allah na gode maka" Ta dinga maimaitawa cikin bandaki hawaye na layi bisa kuncinta. Wanka ta sakeyi dab da asuba da ruwa me dumi sosai,koda ta fito ma'u ta ajiye mata wasu kayan da zata saka. Har zata fita ta bata waje ta canza kayan tace ta zauna,tana jin ma'u kamar jininta,tana jin gamsuwa da dabi'un ma'un. Mutum ce me kamun kai sosai,kawaici gami da kauda kai daga kan komai da bai shafeta ba ko kuma ba'a sanya da ita ba,wannan yana daya daga cikin dabi'un da suka sake sanyawa hankalinta ya kwanta da ma'un. Ko data shirya hijabi da abun sallah ta buqata,ma'un ta bata ta koma ta zauna. Ta shimfida ta tada sallar. Isha'in da bata samu yi ba a dazu ta bayar,sannan ta dora da shafa'i ta kuma zarce da nafilfilun da ita kanta batasan adadin guda nawa tayi ba. Sam sam bata jin koda digon bacci a idanunta,samun kanta tayi da tsananta addu'o'i masu yawan gaske cikin sallarta. Idanunta sun zubda hawaye masu yawan da adazu bata zubda su ba,jikinta yayi wani mugun sanyi zuwa bayan wani lokaci,qafafunta sunsha tsaiwar da zama kawai take da buqata,saita zauna din tana irga tashihi da yatsun hannunta. Tuna abinda ya faru da ita dazun kawai razani yake haifar mata,yayin da kwanyarta tayi nisan zango wajen tunanin waye yake da alhakin zamewa mashkur jagoran daya risketa har cikin dakinta. Tayita qoqarin tuna abinda ya faru bayan zubewarta amma ta kasa tuna komi......abinda kawai take iya tunawa sanda ya shigo dakin da fadawa jikinsa da tayi tana neman tallafi cikin kubcewar numfashi. Kiran farko dana biyu duka akan kunnenta akayi shi,bayan sauran masallatai sun tada tasu sallar sai itama ta miqe ta bada nata faralin. Ci gaba tayi da zama still a wajen......tana tsammanin wai ko zataji bacci amma babu shi ba alamarsa. Wani firgici takeji har tsakiyar zuciyarta wanda bada taimakon hailala da takeyi zuwa yazu batajin zata iya zaman dakin ma gaba daya. Sanda gari yayi haske ta kalli ma'u dake gefe a zaune,qaunar ma'un da darajarta yana qaruwa cikin idanunta. Sam tana lura da ita batayi bacci ma itama "Kije ki huta ma'u.....baki samu bacci ba kema" Sabreen ta fada muryarta a karye da wani irin sanyi da bata taba yi ba. Dan murmushi ta saka tana gyara zamanta "Ba wani damuwa.....bai kamata ai na barki ke kadai ba......saidai ko idan kina buqatar cin wani abu?" Kai sabreen ta girgiza mata "Bana buqatar komai.....kije kidan rage baccin ma'u ki kintsa......kya dawo daga baya,bana buqatar komai". Kai ta jinjina sannan ta miqe tana mata sallama ta fice. Qarasa shafa addu'o'inta tayi ta miqe tana son jin qara watsa wani ruwan dumin ko jikinta zai qara yi mata dadi. Wannan karon saita taka zuwa bakin qofa ta murza lock dake jikin qofar kamar me tsoron maimaituwar abinda ya faru daren jiya ya sake faruwa,sannan ta juya a hankali tana wucewa toilet din. Tare dasu Jordan da farouq ya kawo suka wuce sallar asuba,wadda duk da qarancin baccinsa hakan bai hanashi samun sallar asuba ba. Tun daga fitarsu zuwa dawowarsu su kansu sun fahimci sam yau ba'a mode dinsa yake ba. Idan kai baqo ne a rayuwarsa ba lallai ka fahimci lokutan walwalarsa dana bacin ransa ba......kawai zai zame maka kaman daya ne saboda rashin fara'a da bai da ita......amma gasu da suke tare dashi tsahon shekaru,suna iya fahimtar walwalarsa da akasinta dukka qarqashin dabi'arsa me kamanceceniya da juna. "Mu qarasa ciki jordan" Yace da jordan din bayan sun shigo ainihin farfajiyar gidan. Ba musu ya takewa uban gidan nasa baya suna takawa zuwa dakin da ya bada umarni a ajjiye masa su. Duk da kusan dabi'ar gidan shuru ce,amma a yau tana jin gidan ya sake zama shuru gaba daya. Hakan yake don tun daga gate din farko na gidan zakaji gidan yayi wani mugun shurun da ko tarin wani babu. Zaka rantse da Allah mutuwa akayi cikin gidan saboda yadda kowa ya sake shiga nutsuwarsa. A mugun kasalance da wani irin rashin kuzari ta shirya cikin atamfa dinkin plain zani da riga,wanda babu wani ado da akayi mata ko guda daya face qwarewa da gwanancewar dinki daga telan nasu. Dare daya amma gaba daya ta fada,tayi wani rama da ta bayyana har a qasusuwan wuyanta,fuskarta tayi fayau,inda ya fashe a jiya sai yanxu ya fito sosai ta ganshi. Tsaga ce 'yar siririya bame yawa ba,fuskarta tayi wani fayau kaman wadda tayi zazzabin dare. Koda ta kalli fuskarta gaba daya sai taji zuciyarta ta karye,ta koma da baya a hankali tana sake tuna yadda mashkur ya fado mata daki. Duk wanda wani bala'i ya sameshi kalleshi kawai......ashe fiye da haka matan da ibtila'in fyade ya fadawa suke ji?. Raurau idanunta sukayi,can qasan ranta sai ta samu kanta da godewa Allah da ya bata ikon tsame mata da yawa da suka fuskanci ibtila'i irin wannan zuwa sauyin rayuwa daya kawo musu sassauci da rangwame. Qasa tayi da kanta,daidai lokacin da taji ana mata knocking. A nata zaton ma'u ce......wannan ya sanyata kanta tsaye ta nufi qofar ta kuma bude tana bada hanya,saidai a maimakon ma'u anni ta gani,gefanta kuma amna ce tsaye tana riqe da purse din annin. Wani irin nauyi da bata taba jin irinsa ba ya saukar mata,tayi qasa da kanta tana basu hanya. "Ai jikinma yayi kyau.....basai mun shigo har uwar daki ba,mu koma falo mu gaisa a can" Anni ta fada cikin dattakon nata tana juyawa da nuna alamu na surukuta "Da kun qaraso din dai anni" Sabreen ta fada adan kunyace da nufin tsaida annin "A'ah qaraso nan din sabreen.....ki fito a hankali karki gaggawa" Anni ta fadi tana qara yin gaba,amna da abun yaketa burgeta takeson tayi tsokana nata binsu da dariya. Dukka hannayensa ya zube a aljihun wandonsa yana qare musu kallo cikin quntataccen qaramin store din ajiyar kayan aikin sola dana engine din gidan idan ya samu matsala. Daga daren jiya zuwa yau idan ka kalli fuskokinsu sai kace basu bane,kada ma mashkur daya kwana a daure yaji labari. A duk sanda ya kalli mashkur din shi kadai yasan abinda yakeji......har yanzu maganganunsa sunqi daina amsa kuwwa a kuwwa a kunnensa.......har yanzu ya gaza daina tuna sunyi gamayya a daki guda qarqashin abun shaye shaye guda. Taku biyu yayi y is gaban qofar yana duban mashkur din "Waye ya aikoka?,ko kaine ka aiko kanka da kanka makasarka?" Kai ya mirgina alamun eh.....koda meye zai faru bayajin zai iya buda baki ya fallasa wannan sirrin.......sirrin da idan har ya bari ya fita to tabbas shima ya gama jin dadin rayuwarsa har gaba da abada koda yayi escape. Abu ne bisa sharadi da yarjejeniyar da aka qullata bisa masaniya da kuma abinda zai faru a qarshe. Sosai fu'ad ya zuba masa idanu yana karantarsa,yanayinsa ya tabbatar masa bai shirya fadin gaskiya ba duk da baqar wahalar da ta nuna kanta a tattare dashi. Bayajin zai iya wahalar da kansa tsaiwa yana batawa kansa lokacin tambayarsu,yana da wadanda zasu tafi masa dasu har su gane kuskuren da suka tafka na shiga gonar da ba nasu ba. Hannu kawai ya daga ya yiwa Jordan alama,Jordan din ya jinjina kai sannan ya juya yana fita hanyar waje da sassarfa irin ta majiyin qarfi,cikin qasa da minti biyar sai gashi sun shigo da wani. Kakkauran mutum ne,me qiba da madaidaicin tsaho,yana da baqar fata data haska sosai cikin color din uniform din 'yan sandan dake jikinsa. Maqale da jikin rigar rubutun sunansa ne S.nuhu,wanda iya rank dinsa zai nuna maka cewa shine commissioner of police na jahar gaba daya. Salute na juna sukayi shi da fu'ad din,sannan yace "Yallabai yace idan da damuwa ayi gaba dasu" Kai fu'ad ya jinjina yana baro jikin qofar yana takowa a hankali gami da dubansa "A wuce dasu a ajjiyemin su,har sai zuwa sanda na buqacesu". Kai s nuhu ya gyada cikin girmamawa,daga yanda fu'ad yayi maganar ya gama fahimtar komai. Suna girmamashi kaman yadda yake girmamasu,tun daga can copral har zuwa matakin qarshe na samansu,wannan ya sanya basuyi qasa a gwiwa ba suka bashi kyautar jami'an tsaro cikin mutanensu,mutum ne me qoqarin kiyayewa da mutunta doka. Yana da qarfin mulki dana dukiyar da zai iya komai da yaga dama musamman a yanayi irin na qasarnan da zaka iya komai ba komai bane,amma baya yin hakan,komai din yana qoqarin ganin ya azashi akan mizanin daya dace. "Don girman Allah ka taimakeni.....kayimin sutura.....yallabai ni na fadi gaskiya,na fadi gaskiyata......iyakar gaskiyata kenan". Hanzari ya fada yana hade Hannayensa waje guda yana kallon fu'ad da tuni ya soma wucewa xuwa cikin gida. Ko muryarsu bayason ji bare yakai ga kallon fuskokinsu,don haka baiko waiwayo ba bare ya saurareshi. CP s.nuhu ya daka masa tsawa "Miqe muje......ku daukeshi ku samin a mota,mutanen banza kawai......banda ma me jadda din kuka samu waye kamanshi da zaku keta masa haddin gida ku shiga ku wayi gari haka da sauran lafiyarku?,ba a nan zamu gane gaskiyar taka ba......muje don ubanka" Cp ya fada shi kansa abun yana masa takaici. Sam baisan da zuwan annin gidan da safen ba,don haka kanshi tsaye ya shiga falon hankalinsa yana ga samanshi. So yake ya isa ya kulle kansa don baya buqatar ganin kowa kaman yadda bai buqatar hayaniya ko dogon magana sam sam. Saidai yana sanya qafarsa a falon yaji muryar annin sanda take fadin. "Allah ya qara lafiya......yasa kaffara,saiki dinga kula da jikinki da kyau,Allah ya inganta". Murna ta kama amna,duk yadda taso cinye maganar amma sai data fito " Anni......wai.....wai hamma shima ya kusa zama daddy?". "Ungo nan" Anni ta fada tana watsa mata yatsunta biyar,saita saka hannu ta qunshe bakinta tana dariya. Shikam daga shi har sabreen dake zaune daga gefe maganar tazo musu a wani irin ba zata. "Allah ya inganta?....zama daddy?,wata qaryar ta gilla musu kenan?" Ya fada qasan ranshi yana yamutsa fuska gami da watsa mata wani irin kallo duk kuwa da cewa yana nesa kadan dasu,sannan dukkansu ba wanda yasan ma ya shigo parlor din. Kai ya jinjina wani abu yana tsaye masa a wuya "To yaushe tayi cikin?" Yaji tambayar ta taso daga ransa,take yaji kansa ya qara masa wani nauyi saboda wani tunani da yazo ransa. Dukka juriyarsa da yakejin kamar tana sulalewa ya tattaro yana sake maimaita sallamarsa,suka daga kai dukansu suna amsawa banda sabreen da tayi qasa da nata idanun tana jin sam sam bata sha'awar dubanshi. Gefan anni ya zauna kaman yadda ya saba a gida,duk sanda zai iso gabanta gefan ta nan ne wurin zamanshi. Tuni amna ta kama kanta tana gaidashi cikin tsoro,don tasan zai wahala baiji abinda ta fada ba. "Ina kwana?" Sabreen ta samu kanta da fadi duk da bata dubeshi ba,haka kawai takejin wani irin nauyin anni. "Lafiya qalau.....ya jikin?" Ya furta a dake yana dan duban fuskarta kadan wajen daya lura a jiya ya fashe,baiga komai ba don ta rufe wajen da dan kwali,sai ya dauke dubansa daga kanta zuciyarsa tana masa zafi. Ba abinda ya hanga saman fuskartata sai guntuwar wiwin daya gani jiya a bakinta,zuciyarsa ta sake matsewa,baya jin zai samu wani nutsuwa a zuciyarsa muddin bai samu cikakken bayani abinda yake faruwa ba ko kuma ya farun. Hankalinsa ya maida kan annin ya soma gaidata cikin nutsuwa da girmamawa. Yaji dadin yadda farouq bai daga mata hankali ba ya gaya mata abinda ya faru a gidan ba jiya da daddare,yadai gaya mata kawai sabreen dinne bata da lafiya "Allah ya qara lafiya.....sai ka kula da ita sosai.....inajin idan zai yiwu ma nabar amna a gidan,don a yanayin mace irin haka zaman kadaici qara miki ciwo kawai yakeyi". Dan satan kallon anni yayi,ya fuskanci tunda ta zauna a wajen kawai kallon me ciki take yiwa sabreen din,inda anni tasan cakwakiyar da yake ciki zama zatayi tayita masa kuka. Kwata kwata a birkice yake kan lamarin,kusan komai nema yake ya dagule masa,yana jin kamar kwanyarsa ta daina aiki yadda ya kamata. Ya lumshe idanunsa yana jin ciwon yadda mahaifiyarsa ta xama silar qulluwar alaqa tsakaninsa da yarinyar da kullum munanan boyayyun halayenta sake bayyana sukeyi. "Ashsha......da kinyi zamanki ai,ina ke ina hidima damu ke da ba cikakkiyar lafiya gareki ba?" Anni ta fadi sanda Sabreen din ta fito daga kitchen ta ajiye mata tray dake dauke da spicy black tea soyayyen qwai da kuma farfesun kan rago wanda ta yi tun shekaran jiya waccan amma ta kasa ci,kasancewar ita din cin abinci ba damunta yayi ba. Zataci din amma gutsul gutsul kamar na dan qaramin yaro,shi yasa ko yaya ita ko ma'u suka girka abu sai yayi musu yawa. Sallamar da akayi daga bakin qofa ya maida hankalinsu can. "Sannunku dai.....gafaranku" Zuwairan ke fadi tana rarraba idanu. Zuciyarta cike fal da fargaban kada shigowarta ya zama silar barinta aiki.....amma kuma tana jin relief na wani fannin idan ta tuna tana da assurance na bazaice komai ba muddin annin tazo gaidawa. Zubewa ta gaidashi,amsawa daya yayi mata,ganin hakan sai ta tattara hankalinta ta maida kan annin tana zuba gaisuwa. "Ya mukaji da wannan abu?" Zuwairan ta fada duk da a tsorace take. "Ke!" Fuad ya fadi da kakkaurar muryarsan nan dake saurin isar da saqo gun wanda aka kira saboda zurfin muryar da wani irin kaifi *_DUNIYATA LITTAFIN KUDI NE(PAID BOOK),KAI TSAYE KI TUNTUBI WANNAN NUMBER_* 08187255862 𝐃 𝐔 𝐍 𝐈 𝐘 𝐀 𝐓 𝐀 _Zafafabiyar_ ̶B̶O̶O̶K ̶2 ⱧɄ₲Ʉ₥₳ 𝙋𝘼𝙂𝙀 62 62 "Eh......na'am" Ta fadi adan zabure "Kin taba samun matsalan qwaqwalwa?" Ya tambayeta kai tsaye da wani kallo da yaso rikita duk lissafinta. Kai ta fara girgizawa "Ranka ya dade.....aah" "Good" Ya jinjina kai "Bacen a gun" Ya fada a taqaice wanda yana kaiwa qarshe tana miqewa da hanzari gami da cewa "Tuba nake.....tuba nake". Daga shi anni har amna binta sukayi da kallo,a mamakance anni ta maido dubanta kansa bayan ta fice "Allah me mutane.....ina ka samo wannan Muhammadu?" "Maamah ce....." Ya fadi a taqaice yana jin wani abu game da matar tare da bin hanyar da ta wuce da kallo kaman tana wajen har a lokacin. Tun bai qarasa ba ta fahimci inda zancan ya dosa,kai kawai ta gyada tana fadin "Allah ya rufa asiri......mu zamu wuce.....diyata" Anni ta fadi tana murmushi. Qasa sabreen ta sakeyi da kanta tana dan qaramin murmushi. Karon farko idanunsa suka soma kaiwa kanta,karon farko kuma yaga wani abu me.kama da murmushi akan fuskarta......hakanan lokaci na farko da yaga wani alamu na wata aba wai ita KUNYA a tare da ita. Tsaki yaja qasan ranshi,bayajin wannan abun da takeyi har qasan ranta take yinsa,yadda ta wani sunkuyar da kanta,abinda bai taba gani ba a tare da ita sai yau. "Allah ya qara sauqi kinji.....ki kula da jikinki da kyau" Anni ta fadi tana jin yaqinin kamar abinda dai take hasashen ne yake tare da sabreen. Har cikin zuciyarta takejin yarinyar,tana kuma jin kamar ta taba ganinta a wani wajen kafin yanxu,amma kuma ta gaza tunawa. "Ameen anni.....na gode" Siririyar muryarta da yau kadai tayi wani irin laushi ta fito tana furta hakan har yanzu kanta a qasa. Dukkaninsu suka takawa anni xuwa inda lafiyayyar BMW dinta take jiranta da masu tsaro lafiyarta mutum biyu "Zamu tafi tare da amna din.....amma anjima da dare in sha Allah zata dawo,sai kinfi jin dadin xaman......nasan halin Muhammadu....indai kin ganshi gida zaune to saidai annual leave dinshi yazo ko kuma baida lafiya da gasken gaske". Haka kawai ta samu kanta da kallonshi ta gefen idonta. Duk da ba dogon zama sukayi ba,gajeran zama ne maras dadi da ma'ana,zaman da baida wani alqibla ko kadan,amma ta karanci dabi'u masu yawa tattare dashi. Aiki kaman baisan ciwon kansa ba,kamar kuma yafi kowa sanin muhimmancin lokaci,bata taba ganinsa ba system ko takardu ba.....sannan zaman kadaici baya damunsa sam sam. Suna a tsaye motar ta soma motsawa tana fita ta tafkeken gate din gidan. Idanunta akan bayan motar,tana jin kaman ta hanasu tafiya ita da amna din,dan wanzuwarsu na qananun mintuna kadai sai taji kaman an rage mata wani nauyi da takeji a zuciyarta. Lallai maraici babbar masifa ce,ciwo ne wanda bashi da magani har xuwa randa naka ajalin xai ruskeka,wanda ya rasa uwa shi daya yasan irin asarar daya tafka da ba zata fadu ba. Sai da motar ta gama ficewa tas sannan ta tuna a inda take a tsaye,da kuma wajen waye take?. Ba tare data juya ta kalli inda yake a tsayen ba ta juya a hankali tana komawa ciki. Da kallo ya bita ranshi yana sake masa susa......idanunsa suka sauka kan hips dinta da suka bayyana sosai saboda mayafin dake saman kanta bame girma bane,take zuciyarsa ta wullo masa hoton hijabinta na jiya da yasha cukuikuiya,wani zazzafan abu me tauri ya taso masa da ya sanya ya gaza riqe kansa,sai kawai yabi bayanta yana jin ya zama dole lallai lallai yasan kome. Tana dab da isa qofar da zata sadata da parlor dinsu na farko ya cimmata. Bata zaceshi ba ta tsinceshi a gabanta. Kallon kallo suka yiwa junansu,wani irin kallo na tsakiyar idanu,tsakanin shi da ita kowa zuciyarsa na dauke da wani irin nauyi da baisan yadda zai rageshi ba. Ta dauka zata iya jurewa ci gaba da kallon tsakiyar idanun nasa amma sai taji ta sare nan da nan,ta janyesu bugun zuciyarta na daduwa wanda batasan meye sila ba. Qasa tayi da kanta,so samu ta rabeshi ta wuce saboda fushi take gani cikin idanunsa,ita kuma yanzu qirjinta bazai iya daukan fada masifa ko tashin hankali ba hakanan. Kai kawo kawai adams apple dinsa keyi alamun akwai abinda yaketa qoqarin hadiyewa,jiyan ce kawai ke dawo masa,yana tuna sanda ya dagata towel din jikinta daya xame warwas a qasa,daga ita sai hijabi. Sai daya tabbatar yayi babban aikin rage fushinsa da abinda yakeji sannan ya soma magana,cikin bacin rai amma kuma yanata kokawar kalmasa harshensa,don bayani yake buqatar ji,duk da cewa ta kowacce fuska.....duk kuma inda ya juya.....kowacce hujja idan ya daga,ya tattaro ta nan data can ba abinda take sake nuna masa sai ainihin WACECE ITA. "Wancan lokacin.......na taba ganinsa cikin hotel a abuja yana cigiyar karuwarshi da suka kama daki,ta kwashe masa kudade masu yawa kwatankwacin yadda ya faru da kamfanin JADDA DIAMOND CHORES RESOURCES,sanda naga fuskan wayar ba kowa bace a ciki sai KE!......Wanene shi?,ya akayi ya shigomin cikin gidana?,cikin dakin da aka gina da tsaftatacciyar dukiya ta halak?". Wani irin duka tambayar tasa tayi mata,wadda tazo mata hade da labarin da batasan ya faru ba......eh ta taba binsa abuja.....kuma aikin mashkur kusan shine aiki na qarshe da tayi har yau kuma bata sake sha'awar maimaita wani abu makamancinsa ba.......amma yaushe ya fiddo hotonta ya nunata a matsayin karuwa yana cigiyarta?. KARUWA kalma mafi muni da tafi tsana taji ta gilma a kunnuwanta......duk yadda takai tsakaninka da ita muddin xaka kira wannan sunan a gaban fuskarta......to takan iya manta ya kuke da ita?. "Am asking you......" Ya fada yana jin ya soma hasala ganin shurun da tayi kamar ba da ita yake magana ba. "Ban sani ba......." Ta bashi amsa muryarta tana so ta fara rawa. Me zata gaya masa wanda zai sanya ya fahimceta?. "Baki sani ba kaman yaya?,ya shigo har dakin ba tare an fasa kowanne gini na gidan nan ba......ya shigo dakinki ba tare da kinyi yunqurin kiran koda security daya na gidan nan ba......ya shigo dakinki daidai lokacin kwanciyar baccinki?,a sanda kike daure da towel kadai da hijabi?" Ya qarasa maganar yana qarasawa dab da ita,yana kuma kaiwa qarshe a tsawace har sai data lumshe idanunta ta kuma gaza budesu. Tsawa......tsawa,bata son tsawa,bata qaunarta,tsawar ma daga wajen d'a namiji.....wanda tuni ta karanci sun jima da raina ajawalin mata. Wani abu data jima da shawa kanta alwashi,raini.....wulaqanci.....izgili da toxarci na da namiji,ita ko 'yan uwanta ba wanda zata lamunta ya daukesu. "Ban sani ba nima" Ta sake maimaita masa don da gasken batasan yadda akayi mashkur ya shigo ba. "Harda wayar daya baki kenan itama ita ta kawo kanta?!.....nace ita ta kawo kanta?!!!" Ya fadi da qarfi kaman yana shirin fasa mata kunnuwa. "Stop it!.....wanne kakeso na amsa maka?,wacce tuhuma kakeso na baka amsarta?!" Itama ta maida masa muryarta na rawa,oily eyes dinta suna qara walainiya cikin hasken ranar daya fara dagawa. "Ni kikewa shouting?" Ya tambayeta da tsananin mamaki,saidai kuma qarar wayarsa ta janye magana ta gaba da yaso fadi. Bai fiya daga waya a cikin irin wannan yanayin da yake cikin tsananin fushi ba......amma yana expecting kira me muhimmanci daga gurin wani dan kasuwa mazaunin qasar ivory Coast,dole ya ciro wayar. Shi da ita dukansu akan sunan FAREEDA KHALEED MUSTAPHA ya sauka,ita ta fara janye idanunta tana jin wata wani fushinta yana ninkuwa. Ya sanyata a gaba da tarin tambayoyinsa amma shi a daidai lokacin karuwarshi ko yarinyarsa.....batasan da wanne suna zata kirata ba ita ke kiransa?. Ta nashi bangaren banda muhimmancin da wayar ke dashi a wajensa tabbas ba abinda zai hanashi tarwatsata ita kanta wayar a wajen bama fareeda kawai ba. "Sorry sir" Yaji an fada da sauri,abinda yakai hankalinsu kenan wajen. Me sunan malam ne,da sassarfa yake barin wajen saboda kunyar yadda ya samesu a tsaye dab da juna,baisan kuma zai samesu a hakan ba da bai biyo ta wajen ba. "Zo nan" Ya kirashi a nutse yana duban hannunsa dake dauke da newspaper daya saba ajiye masa duk safiya daga kamfanin jaridu daban daban. Sunkuyawa tayi ta zame ta gefansa tana takawa don barin wajen,haka kawai taji bama zata iya zama ta fuskanceshi ba sam. Kwata kwata bata yarda dashi ba Shima.....wacece faridan?,meye alaqarsu da koda yaushe layinsa cikin karbar kiranta yake?. Yana jin wucewarta amma bai waiwaya ba don hankalinsa yana kan me sunan malam. "Good morning sir" Ya sake gaidashi cikin girmamawa yana rusunawa ba tare daya miqa masa newspaper din ba kaman yadda ya saba,duk da yawancin lokuta ma yana samunsu ne a daura da dining suna jiran fitowarsa,idan ga kammala dubawa kuma zai kwashesu sai kuma fitowar gobe. "Morning.....how you doing?" "Fine sir" Still ya kuma amsa masa amma ba alamun zai miqa masa su. Abun yadan bawa fuad mamaki,yana shirin miqa masa hannunsa don ya bashi kira ya kuma shigo masa. Kai tsaye aka gaya masa farouq ne don haka ya daga ba wani bata lokaci "Good morning dude" Farouq ya furta kaman yadda ya saba masa,saidai kuma daga can qasan muryarsa kaman yana iya tsinto wani abun "Morning......mun tashi lafiya?" "Fine.....ya jikin naka?,ka fita ne ko ka sauko daga stairs?" Duka farouq din ya cure tambayoyin ya masa,abinda yaja hankalin fu'ad kenan. "Ban fita ba......na sauko qasa na rako anni yanxun xan koma ciki". "Good.....but do me a favor mana" Ya fada yana fatan idanunsa basuga abinda ya gani ba. "Ehnnnnn" Fu'ad ya fada yana jin zaquwa na jin abinda zai fito a bakinsa. "Kayi skipping duba newspapers na yau mana......instead of that ka bani aron time din muyi magana" Yadda farouq yayi maganan kawai ya sanyashi yasha jinin jikinsa,sai kawai ya miqawa me sunan malam hannunsa yana masa nuni da newspapers din da yake rqe dasu yana kafeshi da idanun nan nasa da kwarjini ke cike dasu kullum ba tare da ya sauke wayar a kunnensa ba. "Kowanne lokaci na yini na zan iya baka farouq,not the only news time" Ya bashi amsa sanda me sunan malam ya miqo masa newspapers din da hannu biyu cikin mutuwar jiki,ya kuma janye daga wajen da sassarfa don bazai iya tsaiwa yana dubansa a sanda yake kallon labarin dake buge a jaridar ba. *_DUNIYATA LITTAFIN KUDI NE(PAID BOOK),KAI TSAYE KI TUNTUBI WANNAN NUMBER_* 08187255862 𝐃 𝐔 𝐍 𝐈 𝐘 𝐀 𝐓 𝐀 _Zafafabiyar_ ̶B̶O̶O̶K ̶2 ⱧɄ₲Ʉ₥₳ 𝙋𝘼𝙂𝙀 63 63 "Wannan abun kawai nake buqata please" Farouq ya maimaita sanda ya shiga motarsa dake farfajiyar gidan. So yake yaja maganan da tsaho sannan ya cimmasa kafin ya duba abinda ke faruwan saidai sanda yake bashi amsa na qarshe yana bashi amsar ne sanda idanunsa suka sauka akan tittle na labarin da yaci shafin farko gaba dayansa na jaridun guda biyu. *_TSINTAR DAMI A KALA_* _BABBAR JARABAWA......SHIN KUSAN WACECE ASALIN MATAR MATASHIN MILLIONAIRE DINNAN MAMALLAKIN KAMFANINNIKAN DAKE SARRAFA GWALA GWALAI?_ "Farouq.....you have my time,amma kafin sannan......" Maganar ta yanke masa sanda makeken hotonta ya biyo bayan title din ita da mashkur. Hoto ne da aka daukeshi gaban wani hotel da sunan kawai ya iya kalla ba tare daya tantance wanne bane.......sanda ya bude mata murfin motar ita kuma tana qoqarin fitowa a motar yana riqe da handbag dinta. "Hasbunallahu wa ni'imal wakil" Ya fada yana jin dukka gabbansa suna daukan dumi kafin daga baya kuma suyi wani irin sanyi kaman ba'a jikinsa suke ba. _mrs muhammad fu'ad jadda sabreen ahmad_. Baya jin idanunsa zasu iya ci gaba da kallon abinda ke gabansa,sai kawai ya hade newspapers din waje daya ya curesu a hannunsa yana takawa zuwa cikin gidan ba tare daya tsaya tuna cewa magana suke da farouq ba,kuma yabar farouq din akan line na waya. Shuuuu din da farouq yakeji ya sanyashi qarfafa zarginsa akwai abinda ya faru,sai kawai ya aje wayar ba tare daya kasheta ba,ya tada motar da wani irin hanzari wanda yanayin gaggawar da security na gidan suka ga yanayi ya sakasu dage masa qofa ya fice tun bai qaraso ba. Bazaice ga wani abu da ya faru daga sanda yakai kansa samansa ba banda azababben ciwon kai da yake masa kutufo kota ina. Ba abinda bakinsa ke furtawa sai Astgafirullah yana me kyautata zaton akwai wani abu daya aikatawa ubangiji wanda ba daidai ba shi yasa ya jarabceshi da wadannan abubuwan. Dukka komai akan yarinya daya?.......yarinyar da koda ta zame masa zabi a nasa qashin kan hakan ba lallai ya tabbataba banda miqewa da kafewar maamah akan lamarin?. Da qyar ya iya amsa sallamar farouq sanda ya bude smart door din ya qaraso cikin parlor din idanunsa akan fu'ad. A yadda yaga idanunsa sun jirkita ya tabbatar labarin ya gama ruskarsa. Da idanu yabi farouq din,har zuwa sanda ya qaraso,ya tsugunna ya debi duqunqunannun jaridun ya bude ya kuma rufesu a take. "Da gayya aka buga wannan news din......." "To menene qaryar da sukayi a ciki?.....ban karanta sauran labarinta a qasa da suka saka ba.......amma wanne ne qarya farouq?" Maida dubansa yayi kan fu'ad da yake dubansa kai tsaye. A zahiri jijiyoyin kansa ke tashi sosai har sun nuna ta farar fatarsa,wanda abadini yake nuna ciwon kai yakeyi sosai,irin ciwon kan da ya dinga addaba masa sanda yake fama da matsalar depression dinsa,wanda ya tabbatar ya jima rabonsa dashi..... Sakin baki yayi yana kallon fu'ad din daya fara magana cikin sanyi saidai akwai zafi me yawa a kalamansa. "Stop dude.....ina gaya maka.....don't judge book by his cover.........ka daina judging mutane haka" "Judging nasu nake ma?,bayan ina da full details na evidence akan duk maganan da nakeyi farouq akan yarinyar?" Yayi maganan da sanyin dai,amma lafuzzansa na nuna zallar zafin da yakeji. "Evidence kadai bazasu tabbatar da hakan ba.......kayi managing personal boundaries tsakaninku kaman na kowanne miji da mata,akwai buqatar wani sensitive......" "Haba mana!" Fu'ad da yakeji zuciyarsa na matsewa kaman zata fashe ya tsaida farouq yana zama sosai yana jin jiri daga inda yake zaunen. "Kada bakinka yakai nan wajen.......bakasan wacece ita bane farouq?,bakasan sunan da kowa yake kiranta dashi ba?,baka gani jikin newspapers ba?" "Na gani.....na kuma sani......kuma ka rigani sanin haka kace zaka daukota ka gyarata......ya akayi ka kasa fu'ad?" Ya jefa masa tambayar yana riqe habarsa. Kansa ya jijjiga sosai yana duban farouq "Ban kasa ba......bazan kuma kasa ba......abu daya kemin burki.....duk sanda na kalleta sai naji tayi qanqanta da yawa nayi mata kalar azabobin dana tanadar mata......tayi mitsitsiya na sanyata a prison din dana shirya mata......amma duk sanda ta aikata wani abu kota bullo da wani abun........sai naga nine naketa kuskuren kallon tayi qanqanta......a abinda zuciyata ke rayamin wannan karon......duk hukuncin da yazo na dauka a kanta a tunanina na qarshe dashi zanyi amfani......" "Banda divorcee......" "Harda shi idan ta kama" Ya fada confidently. Ido Farooq ya zuba masa kawai,ga mamakin fu'ad sai yaga ya saki wani irin murmushi yana girgiza kai. Shima duban farouq din yake kafin yaji murmushinsa ya bata masa rai. Bayajin a yanayin da yake ciki ya kamata wani abu me kama da murmushi ya fita a fuskan farouq,don haka ya miqe tsam yana dosar bedroom dinsa. Da hanzari farouq ya miqe yana kiransa "Wait dude.....wait" Don ya tabbatar wannan bedroom din nasa me smart door idan ya shiga ya rufe baka isa ka bude ba muddin bai sakaka cikin wadanda zasu iya budeta ba. Bai saurareshi ba ya shige dakin abinsa,da qarfi ya rufe qofar yabar farouq a nan a tsaye. A yanzun da baya ganinsa sai murmushinsa ya ninka na dazu,bayan minti uku yayi qoqarin daidaita kansa,ya matsa yana daukan telephone na falo din ya kira cikin dakin nasa. Yayita kira yana jiyota tana ringing,kaman bazai daga ba kafin ya daga daga baya,ya sakata a kunne ba tare da yace komai ba. "Am really sorry dude.....na hango wani abu ne daban da yake durfafoka da matuqar qarfi fiye da qarfin guguwa......amma it seems like baka ganshi ba baka kuma fahimceshi ba......anyways kayi aiki da hankalinka da intelligent dinnan dana sanka dashi.......am always free,and then it's time to act for koma waye behind all these issues......na tabbatar akwai wani abu boyayye......think wisely......am always by your side.....take a rest,but please kasha magani". Sanyaya ranshi sosai maganganun farouq sukayi,yayi shuru kawai yana saurarenshi bai iya ce masa komai ba......shi kansa baisan me yasa a bangaren nan kaman qwalqwalwarsa bata iya aiki daidai ba?. Yana jin kamar ya gaji......yana buqatar hutu da gaske na jiki dana kwanya "Am tired farouq......I'm feeling burnt,i need some time to unwind and focus on my well-being......kayi magana da saddiq.....i want him to schedule my annual leave cikin kwana uku". "Kowa ma lokacin hutunsa yazo......International gateway to Maldives" Ya furta yana motsa labbansa gami da jefa hannunsa sama yana kwatanta yadda jirgi yake cillawa sama yayin daya cirata daga qasa. "Zan kawo nesa zuwa kusa......zan dawo da mafarki zuwa gaskiya......komai zai warware.....zan kuma baka mamakin yadda zan juya maka rayuwarka dare daya" Farouq ya fada yana dariya kaman mummunan abu irin wannan bai faru ba. Kawai wani nishadi yakeji qasan ransa idan yayi imagination na yadda komai zai kasance,sai yaji kawai ya qagu shi Kansa lokacin yayi,sai ya juya ya tattare key da wayarsa yana maidawa aljihu ya soma sauka yana barin gidan,ko saddiq dinma bazai nema ba.....shi zai shirya komai,sai komai din ya kammala sannan kowa yaji ya gani. *_tom......me karatu?,wanne plan kake tunanin farouq yana dashi akan fu'ad?,muje zuwa_* Yana driving a mota amma tunani fal kanshi. Tunda yake bai taba hangen wani abu daya jigata fu'ad komai tsananinsa ba kaman wannan......anya ba burbushin wannan halittar daya tsirowa zuciyarsa kuwa?, wadda kusan itace jigo na kowanne tsanani da wahala da zuciya kan iya shiga akan wani dan adam?. *_DUNIYATA LITTAFIN KUDI NE(PAID BOOK),KAI TSAYE KI TUNTUBI WANNAN NUMBER_* 08187255862 𝐃 𝐔 𝐍 𝐈 𝐘 𝐀 𝐓 𝐀 _Zafafabiyar_ ̶B̶O̶O̶K ̶2 ⱧɄ₲Ʉ₥₳ 𝙋𝘼𝙂𝙀 64 64 Bayason irin fushin da yakeji cikin ruhinsa da jikinsa gaba daya......yana buqatar yayi cooling down ko yaya ne,a lokacin ayar nan da taxo cikin alqur'ani me girma ta fado masa "Ku saurara.......da ambaton Allah kadai zukata ke samun nutsuwa" "Sadaqallahul azeem" Ya fadi yana miqewa hadi da fara jin sassauci daga tuna ayar kawai. Toilet dinsa ya shiga,ya daura alwala me kyau,sannan ya dawo cikin dakin yana kunna chandelier din dake kafe tsakiyar dakin,wadda ke hade da Bluetooth da kuma fanka me bada sassanyan iskar data banbanta data sauran fankoki. Remote ya dauka ya kashe hasken don baya buqatarsa,ya kuma kunna speaker din dake jiki yana daidaitata da wayarss,take muryar fasihin malamin nan limamin ka'aba wato sheik abdurrahman assudais ta karade dakin cikin sauti mafi tsarki na karatun alqur'ani. Relaxing yayi sosai soman sofa din dake dakin yana jin wani sukuni ya soma ratsahi,kaf a cikin malamai idan akwai wani sauti da yafi so yafi qauna bazai wuce sautin sheik abdurrahman assudais ba,wannan dalilin yaja ra'ayinsa qira'arsa gaba daya ta juye zuwa ta sudais din sak.....da wannan qira'ar yayi sauka,kuma har yau itace a bakinsa. Idanunsa a lumshe yana ci gaba da bin sautin,bazaice yana jin yunwa ba ko kadan,zamansa a haka duk duniya yafi komai yi masa dadi,a haka ya shafe kusan awanni biyu har zuwa sanda wayarsa tayi haske,kira kuma ya shigo wayar tasa. Hannu ya sanya ya jawo yana dubawa,ganin me kiran ya sakashi daukan remote din dake gefansa,ya kashe volume din gaba daya sannan ya daga wayar yana sakata a hands free. "Good afternoon sir......yanzu haka dukka shugabannin gidan jaridan suna hannunmu". Zamanshi sosai ya gyara cikin kujerar yana harde qafafunsa waje daya "Well-done,good job khaleed,akaiminsu housing estate na darmanawa.......by 4 zan fito in sha Allah" "Yes sir" Ya fada cikin tsananin nuna ladabi,bai sake jiran komai daga wajensa ba ya kashe wayar yana ajeta gefe. Bai sake batawa kansa rai da tunani ba ya dauki remote din da xummar qara volume din,cikin ransa yana jin bazai sake barin komai ya bata ranshi har haka ba......ko meye ya faru da ita ita ta jawo......amma fa bazai taba lamunta a taba masa igiyar aure ba,ko kuma sunansa ya fito a ciki ba ko na ahalinsa. Wani kiran ne ya sake shigowa dole ya aje remote din. Asp ne yake kiran,shima bai jinkiri ba ya daga. "Sir........mun sama musu gurin ajiya na musamman......kuma zamu tuhumesu da kyau har sai sun fadi gaskiyar wanda ya aikosu". "Na gode......but inaso ku barmin wannan a hannuna......ku ajiyesun irin ajiyar data dace dasu har xuwa sanda zasu furta wanda ya basu hanya da daman shigowar" "Okay boss...." "Thank you" Ya sake fadi labbansa suna motsawa. Wannan bacin ran da yaketa son hadiyewa still dai ya sake taso masa,ya sanya hannunsa ya shafi kansa. Zai iya cewa tun daga guards dinsa zuwa securities dinsa amintattu ne,bashi da ko kwanto da ko shakka akan koda mutum daya daga ciki,duk da dan adam tara yake bai cika goma ba......kuma wasu daga cikin 'yan adam din masu iya canzawa ne a duk sanda sukaso a karan kansu,walau dalili na son zuciya ko makamancin hakan......amma su kam yayi imanin yadda yake mu'amalantarsu daban yake da sauran yadda masu gida ke mu'amala da yaran gidansu. Kyautatawarsa a garesu ta daban ce kaman yadda qaunarsu a gareshi ta daban ce. To amma a yanzun yadda yakejin zuciyarsa komai ma yana iya faruwa......sannan a yadda yasan ya gidansa yake,abune me wahala a iya keta tsaron gidan a shigo haka siddan ba tare da idon sani ko mataimaki sannanne ba. Volume dinsa ya qaro yana fatan sake samun nutsuwa da daidaituwar zuciyar da zata bashi qwarin gwiwar fita zuwa yammacin. Bai tashi ba sai da akayi sallar azahar,ya daura alwala ya fito don halartar jam'in sallah kaman yadda ya saba muddin yana kusa da masallaci. Dukkanin ma'aikatan kowa rabe rabe ya dinga yi daga ganin fitowarsa. Zukatansu a razane yake abinda ya sanya gidan ya sake daukan shuru gaba daya kamar ba wata halitta a gidan me rai da tayi saura. Bai dawo cikin gidan ba sai la'asar,don ganinsa yau free haka da rana ya sanya masu buqata suka dinga shigowa masallacin. Bai hanasu ba ya zauna ya dinga sauraren kokensu daya bayan daya. Ba wanda ya bari ya tashi a wajen ba tare da gaggwaban abun alkhairi ba,jordan na tare dashi shi ya tashi sauraronsu,sukayi la'asar ya miqe ya wuce gida qirjinsa cike da nauyi. Sai yake sake ganin yadda ubangiji ke tsara rayuwa yadda yaso.......matsalar wani bata wani ba......a yadda unguwar take baiyi zaton masu qaramin qarfi dake neman taimako na shawagi a cikinta ba. Ya dubi kansa sanda yake wucewa ta babban glass door din da zaka taras a gate din farko na gidan. Ubangiji ya azurtashi da dukiya me yawan gaske......lafiya da wadata......saidai ya samu naqasu ta bangaren uwa da mace ta gari,wanda wadannan abubuwa biyun sune jigo a rayuwar kowanne dan adam. Ga wasu can su kuma nasu burin shine INAMA MUNE ME JADDA?,ba tare da sunsan ainihin waye me jaddan ba?,me yake fuskanta?,wacce rayuwa take going through......(wannan ya zamana izina a garemu gaba daya,kafin kayi burin inama kaine wane?,kayi tunanin mene rayuwarsa ta badini?,kayi tunanin wadanne qayoyi ya tattaka da tsinika kafin yakai ga isowa nan inda yake?,ko yaushe idan kaga wani mutum da rayuwarsa ke burgeka,ma roqa Allah ta hanya daban bata hanyar Allah yasa na zama kaman wane ba.....bayan fuskar wane dinnan kawai kake gani bakasan cikinsa ya yake ba,Allah ka kyautata rayuwarmu,ka bamu tsira duniya da lahira)" Da tarin tunane tunane yake ratsowa falon daya xama wani irin shuru. Gaba daya kallon gidan yake wani iri,har a gangar jikinsa yakejin ya gaji da xaman cikinsa. Wuf ya hangi gilmawarta daga kitchen kaman zata kifa tana nufar qofarsu. Har yaci gaba da tafiya wani abu ya sauko cikin tunaninsa "Ke!" Yayi kiranta da wani amon sauti da a take ya tara zazzafar gudawa cikin tumbinta "Na'am......na'am ranka ya dade" Zuwaira ta fada wadda ke rungume da wani abu da baisan meye ba. Hannuwansa ya zube cikin aljihun wandonsa yana qare mata kallo,zuciyarsa tana raya masa wani abu game da ita. Wani abu me kama da xargi tuhuma da kuma rashin aminci a kanta yaji yana tsarga masa. Irin kallon jadda din ba kowanne mutum ke iya jurarsa ba,sai mutum me babbar kurwa,me babbar kurwar ma wanda ya cika da gaskiya da kuma amana,ba wani ha'inci cikin lamarinsa,wannan ya sanya zuwaira ta dinga jin kamar yana karance duk wani sirri dake tattare a qirjinta zuwa cikinta,tamkar ya sanya microscope yana tantance adadin qulla qulla da harqallar data taba shiryawa tsahon rayuwarta,wannan ya qarawa adadin zuciyarta gudu,ya kuma hanata ci gaba da daidaituwa akan qafafunta,saita sulale ta duqa saman qafafunta "Allah ya taimaka.....tuba nake,bansan kana cikin gidan ba ai......da ba'a fito ba,wannana bun daya faru ranka ya dade shine ya hanani nutsuwa.......hajiya naketa son dubawa aga yanayin da take ciki....." "Ke" Ya sake kiranta yana dage dukka girarsa sama guda biyun. "Na'am yallabai na'am......." "Ki tarkata komai naki kibar gidannan cikin qasa da minti goma....." "To an gama ranka ya dade,aisai a komawa hajiya maamah baya goya marayu" Ta furta tana jin wani sassauci da rangwame a ruhinta. A abinda takeji yanzun sallamarta shine babban gatan da yayi mata,duk sanda taji muryarsa sai kowacce kafa ta jikinta ta jiqe da gumi. Sai a yanxu take ganin cewa da gaske xaman gidan jadda yafi qarfinta,wutsiyar raqumi tayi nesa da qasa. A baya tana tunanin duk randa yace taje ya sallameta zataji tashin hankali maras iyaka......amma a yau sai takejin kamar 'yanci ne daga bata zuwa zamowa halastaccen d'a. "Kinsan me?" Ya fada yana sake dubanta,saita dakata tana saurarensa. "Bazan dubi tsufanki ko digon furfura koda qwaya daya dake tsakiyar kanki ba......muddin naxo na sameki kin koma gifan gidan maamah........ki tabbatar daga ranar kin tashi daga aiki......kiyi nesa da ita da komai da kowa daya danganceta.....and hakan bawai xai sakaki kin tsira ba,duk mutumin da yake gidan nan daga kwana uku baya zuwa jiya da abin ya faru baxai tsira ba a waje na......wanda kawai zai tsira shine MAI GASKIYA ". Duburbucewa tayi har akwatin kayan asirin maamah na shirin tarwatsewa daga hannunta. Gab gab gab haka hannuwanta da qafafunta suka dinga haduwa waje daya,wannan wanne irin kalar tashin hankali ne?,wanne irin yaro ne wannan maras imani.... Lallai dole mallakarsa ta yiwa mariya wahala,zuwaira ta furta hakan a ranta sanda take ta qoqarin kai kanta ga sassansu don ta samu ta sulale kaman yadda ya shawarceta. Ayadda ta sanshi tana ganin ko cinye namanka yace zaiyi zai iya......musamman shi daya mallaki masu gidan ranar da babu me tuhumarsa ko bin ba'asin abinda yayin. Gaba daya wunin yau duka hankalinta yana kan wayoyinta,bama ita ba.....hatta da fareeda kowanne motsi nata yake kan social media's tana hasashen watsuwar abun a kowacce kafan sada zumunta. Sanda taga ankai azahar shuru sai duk wata nutsuwa ta soma barin gangar jikinta,hankalinta ya gaza kwanciya kwata kwata,ta kuma shirya kai tsaye ta kira driver ya dauketa zuwa gidan maamah. A sannan ita dinma duban wayar take tayi.......tanaso ta samu wani haske ko yaya yake.......tunda ta zauna take saqa yadda komai zai kasance.......take qiyasta irin tozarcin da zata yiwa sabreen. Lallai sai ta sanyata ta fahimci wutsiyar raqumi tayi nesa da qasa.......ita kanta batasan adadin yawan tozarci da qasqancin da zata sanyata ta fuskanta ba. Mamakinta ya tsananta ainun da rashin samun kai,sai taji ta kasa jira,kai tsaye ta daga waya don kiran fareeda,amma sai fareedan ta hutashe da ita saboda turo qofan setting room din da tayi ta shigo tana taunar chewing gum kaman yadda ya zame mata al'ada,duk kuwa da cewa yau din bata cikin wannan mode din,amma cin chewing gum din ya zame mata dabi'a. "Ke nake shirin kira yanzun.......banga tasirin aikinki ko wani motsi na daban ba" Maamah din ta furta kanta tsaye tana duban idanun fareeda. Idanu tadan xubawa maamah din,mamakin dabi'arta tana dan kamata. Kanta tsaye take magana akan duk wani abu daya shafi buqatarta,ba ruwanta da wata matsalarka ko fuskantar yanayin da kake ciki. Kanta ta dauke tana qarasowa ciki,sannan ta yiwa kanta mazauni saman hannun sofa din tana harde hannuwanta a qirjinta "Wannan shine aiki mafi kashe kudi da nayi......sannan shine aiki mafi jinkirin samun nasara" Tayi maganar tana duban maamah din. "Masu aiki sun kammala.......naki aikin da nawa duka ba wanda ya kawo result me kyau........abu daya ya rage shine,ki kira d'anki ki tuntubi sakamako daga gareshi". Gyara zamanta maamah tayi tana duban fareeda,ta soma fahimtar wasu halayenta da inda dabi'unta suka sanya gaba,bata gayawa fareeda tayi failing a nata agenda din ba.....ya akayi amma ta sani?. "Na yarda har abada yaro yaro ne.......kina tunanin samun galaba akan duk wani lamari daya shafi fu'ad abune me sauqi?,inda kuwa hakanne da bakizo gabana ba......da babu ke cikin babin qaddararmu sam sam" Maamah ta fadi tana duban fareeda. "Duk abinda babba ya hango yaro ko ya hau bishiyar rimi bazai hango ba..........a naki lisssafin kiran fu'ad kai tsaye na jefeshi da salon tambayoyinki abune me sauqi da zai sanya mu wanye lafiya?" Ta qarasa maganar tana duban fareeda data zubawa maamah nata idanun. "Kina iya kiransa ta wata siga daban ki kuma zaqulo bayanan da kikeso......amma zai zama babban kuskuren rayuwarki ki biyo masa ta waccan hanyar taki....." "Amma bisa alqawari da yarjejeniya.......xaki zama tsanina na mallakar fu'ad haka ne?" "Har yanxu ina kan wannan bakan.......amma fidda sabreen daga gidansa aikinki ne......zai iya zama nawa aikin,amma kuma salon aikin nan da yake zamowa ba waji bi". Sun jima suna kallon kallo tsakaninsu,kowanne da kalar saqar dake cikin zuciyarsa game da dan uwansa,kafin fareeda ta fiddo wayar da musamman saboda kiran fuad din ta tanadeta. Da kowacce waya da kuma kowanne layi ta kirashi ba zata sameshi ba saida wannan wayar kadai. *_DUNIYATA LITTAFIN KUDI NE(PAID BOOK),KAI TSAYE KI TUNTUBI WANNAN NUMBER_* 08187255862 𝐃 𝐔 𝐍 𝐈 𝐘 𝐀 𝐓 𝐀 _Zafafabiyar_ ̶B̶O̶O̶K ̶2 ⱧɄ₲Ʉ₥₳ 𝙋𝘼𝙂𝙀 65 65 _Manzon Allah S A W bai taba aibata abinci ba,idan ya burgeshi sai yaci,idan kuma baiyi masa ba sai ya qyaleshi(ba tare daya aibatashi ba)_ Tsaf ya shirya cikin trouser dark blue na yadin vicuna,yayin da sanya black shirt data fidda ainihin kan sassalkar fatar nan tasa me tsananin haske,wadda ta cakuda da hutu da jin dadin dake bayyana kansa cikin kowanne hali yake. Kyakkyawar qasumbar fuskarsa da bata da cika irin ta cukus ta sake qawata fuskarsa da sanya masa kwarjini,tana da santsi kwatankwacin sumar dake lullube saman kansa. Baqa ce sidik kaman gashin girarsa dana idanunsa,hakanan kaman sauran gargasar dake lullube da sassan jikinsa. Agogo fata ya daura a tsintsiyar hannunsa me tsananin tsada daya dace da shigarsa dama tsadar kayan jikinsa,yabi ko ina na jikinsa ya feshe da lallausan turaren nan nasa me taushin qamshi. Tsananin dauriya kawai ta sanyawa ruhinta,tun bayan dawowar amna da batakai magarib ba kaman yadda anni tace taketa qoqarin shimfida walwala akan fuskarta,duk da cewa abun ba haka yake ba daga qasan zuciyartata. Amna din ta dabance,tana da barkwanci da sakin jiki ga duk wanda ta yarda dashi,wannan ya sanya cikin qasa da awa guda taji nauyin dake qirjinta yana raguwa,lokaci lokaci labarun amnan suna sake dauke hankalinta daga yanayin da take ji. Ita ta tilastata da yammacin kan su fito daga daki zuwa kitchen "Wainan fulawa nake sha'awa.......yakumbo ce take mana,ta tafi ganin gida tun wancan satin,muje na gwada ko zan iya please adda" Ba zata iya qin tankwabar da tayinta ba,haka ta maqala hijab saman doguwar rigarta ta bita kitchen din,wanda a qarshe sabreen dince ta hada Mata wainar ta soya mata ta kuma tara mata a warmers. Ta cika da mamakin yadda akayi amnan ta iya girki kala kala amma bata iya wainar fulawa ba. Qwarewar amnan a girki yana bata sha'awa,harma takanji tana sha'awa itama iya kalolin abinciccika. Suna a saman dining tana kallon yadda amnan ke santin wainar fulawan,time to time tana murmushi kawai. Ta sake yarda da gaske rayuwa mataki mataki ce,kowanne da kuma kalar muhalli da hurbin data ajeshi. Duk da fiye da rabin hankalinta bashi a wajen,amma hakan ba hanata jin saukowarsa ba a jikinta. Qamshin turarensa ne ya fara isa ga hancinta,kafin daga bisani qamshin ya fara mamaye parlor din. Cikin dabara ta dauke duban ta daga wajen da yake takowa,tanason nuna sam sam ma bata ganshi ba. Duk sanda fuskarsa zai bayyana a gareta,ba abinda yake tuna mata sai tambayoyinsan nan data tsana,tambayoyin dake matuqar qona masa rai ba kadan ba. "Hamma......barka da yamma" Amna ta furta da murmushi saman fuskarta sanda ta waiwaya ta ganshi,sai ta aje wayar hannunta tana bashi hankalinta gaba daya "Barks lovey dovey" Yayi maganar da wani kwantaccen sauti daya sanya sabreen taji tsigar jikinta ya zuba,take kuma ta daga kanta a hankali kaman me tsoron ganin wani abun tsoro,duk yadda taso ta yiwa idanunta shamaki amma sai da suka fada kan fuskarsa,ta kuma ci karo da wani yanayi dake shimfide saman fuskarsa din. Shi ba murmushi ba sannan kuma ba'a daure fuskar take ba......saidai yana yin ya nuna ya zama very calm ba kaman yadda take ganinsa kwanakin da duka wadannan abubuwan suka faru ba. Zamewa amna tayi tana sake gaidashi bayan gaisuwar daxu,ya amsa yana motsawa alamun xai wuce. Wayarsa dake riqe a hannunsa ta fara bada wani sassanyan sautin sarewa maras hayaniya da yawa,kafin daga bisani sunan FAREEDA KHALED MUSTAPHA ya fita tarwai ta cikin speaker din. Duk yadda taso watsar da sunan daga cikin kunnuwanta amma hakan ya gagara. Sunane data jima tana jinsa akai akai,har kuma ya soma zama a kwanyartata. Maida hankalinta tayi ga amna amma saita gaza ci gaba da hakan,batasan yadda akayi idanunta suka dauketa zuwa fuskarsa ba. Wayar ya daga zuwa fuskarshi yana duban me kiran,sosai ya zubawa numbers din nata idanu,manhajar daya dora kan wayar tasa ke harbawa daga gefan hagu na wayar tana nuna masa abinda fareeda din ke aiki dashi wanda ke fasa duk wani shinge da zai saka number dinta,duk sanda ta jira kiran ya samu damar isowar gareshi kai tsaye. Dan qaramin murmushi ya subuce masa wanda iyakacinsa labbansa,saidai a nata idanun qaruwar murmushin ta gani. Idanunta taja ta lumshe daga kallon dark pink lips dinsa. Batasan me yasa gabanta yayi wata wawiyar faduwa ba,sai kawai taji bata da sha'awar ci gaba da zama a wajen. Tsam ta miqe sanda amna ke ce masa "A dawo lafiya hamma...." Ta fara saukowa daga steps din,a cikin jikinta taji amna din na satar kallonta,wani nauyi ta sakar mata da bisa dole ta motsa labbanta tana fadin "Adawo lafiya" Sosai yaji kalmomin sun zama baqi a kunnensa,har ya motsa kaman zai waiwaya sai kuma baiyi hakan ba ya amsa "Allah yasa" Yana takawa gami da ficewa da takun nan nasa da ta dade da haddaceshi. Wani irin taku yakeyi tamkar namijin toro,zakayi tunanin wani saraki ne,ko kuma yana qawata takun nasa daidai da yadda zaija hankalin masu kallonshi. Ficewarsa daga falon ya bata wani qaramin sukuni,sai ta fasa komawa dakin ta sauka saman sofas din dake falon ta zauna tana maida numfashi. Idanunta ta maida hanyar daya wuce din "Fareeda KHALED MUSTAPHA" Sunan ya dawo mata radam a kunne,murmushinsa kuma ya sake giftawa ta idanunta,ta sake lumshe idonta ta kuma budesu lokaci daya "Waya sani ma ko ita ta kirashi?,wa yasan inda zasuje?" Ta furta can qasan zuciyarta tana tuna irin tuhumomin da take gani a kanta cikin idanunsa. "Waye yasan abinda shi yake aikatawa ma?" Ta sake samun kanta da fada qasan zuciyarta. Ko daya ba zata taba aminta da cewa shi din a tsare yake ba......taga matasa masu tarin yawa da ni'ima da baiwar dukiyar da yake da ita yasu bata taka rabinsa bama......amma qazantar dake cikinsu sai Allah. Kamar dai shi......a haka kamilallen mutum....amma badininsu wata irin danqararriyar qazantace maras dadin gani ko tabawa. "Adda......." Taji muryar amna daga gefanta. Fararen idanunta ta daga tana duban amna gami da katse tunanin dake kai kawo a ranta "Amna" Ta amsa mata murya qasa qasa tana nazartar fuskarta. Fuska ta narke sosai tana zagayowa gabanta ta zauna. "Nace wani abu adda bazai zama shishshigi ba?" Tayi maganar da alamun son ta furta abinda ke bakinta. Qaramin murmushi ta sakar mata don ta bata nutsuwa da gamsuwa akan duk maganar da zatayi "Fadi amna mana" Sai data gyara zamanta tana maida mata murmushin sannan tace "Yaaa saddiq yana bani labarin hamma......duk da na fisu sanin hamma ta wasu abubuwan.......amma ya saddiq kuma zai iya fina saboda shi din PA dinsa ne.....duk inda zai saka qafa a gida ko a office suna tare.......kinsan waye hamma kuwa?,ya yake?" Tayi tambayar da murmushin daya kusa zama dariya akan fuskarta. Numfashi taja a boye tana jin sunansa kawai da amna ta kira yana qara yawaita bugun zuciyarta,inda zata iya zata dakatar da amna daga yi mata duk wata hira data shafeshi......kwanaki kaddan suka rage masa cikin rayuwarta.......tana jiran kawai ranar da zata samu tabbacin su huda sun isa mali lafiya hannun momma bahijja.......a wannan lokacin komai zai tarwatse. "Saikin fada amna" Ta fadi bawai don ranta yana so ba,sake gyara zama sosai tayi ta riqo hannun sabreen "He's a loving and caring partner.he wants a deeply romantic connection with his wife" Ta fada murya can qasa,kaman tana tunanin yana kusa dasu kuma tana tsoron kada ya jiyota. Dukka idanunta sabreen ta fiddo waje tana kallon amna,yadda amna din tayi maganar da wani confidence da qwarin gwiwa ya bawa sabreen mamaki.....can qasan zuciyarta kuma sai taji kaman tanason taja hira kadan da amna din. Abu daya dai tayi amanna fuskar fuad ta gida daban......fuskarta ta gidansa daban.....kamar yadda fuskarsa ta mu'amalarsa ta waje daban,banda haka mutum kaman fuad dinne zata siffanta haka?. "Kina da ja ko adda?......" Ta tambayi sabreen kai tsaye,tana jin tanason tayi hira da ita.......tanaso ta fadi mata abinda ta fuskanta ko ita ta fahimci ba daidai ba "I swear adda........He envisions a future where he and his wife grow old together,hand in hand......ko a gabana wannan yasha fadinsa......musamman idan suna hira na sako da sako shi da BB farouq.......hamma na yana son soyayya,ya kuma cancanceta......hammana yana son kulawa......that's why yakeji dani,komai na hammana daban yake a wajena.....tausayin hamma nakeji coz....He suffered a lot in his life He had a rough past" Ta fada dukka a jere tana riqe da hannun sabreen kaman hakan shine zai saka ta fahimta abinda takeji a zuciyarta na tausayin hamman nata. Baki da idanu kawai sabreen ta sake tana kallon amna,tana sake gasgatawa da imanin cewa eh lallai da gaske wannan mugun yana da muhalli me girma da fadi a rayuwarta......amma wanne irin hardness ne haka ya fuskanta?,mutumin da ya rayu tsakanin iyaye biyu 'yan uwa hudu?,mutumin dake cikin daula da dukiya?. "Believe me adda......please,ki qara akan kulawan da kike bawa hamma,He's passionate about building a strong loving relationship with his wife.......na dade da sanin duk wadda ta samu hamma fuad.....She's the luckiest woman alive and she's incredible fortunate" Murmushi ta samu kanta da subucewa dashi,saita miqa hannu ta riqe amna din sosai bawai don maganganu da yabo a kansa sun burgeta ba,aah......sai don ita din mutum ce me girmama 'yan uwantaka,saboda tasan girman soyayya da qaunar dake tsakanin 'yan uwa me girma ce......itace babbar shaida ta farko akan hakan akan kanta ma. "Duka wannan yabon amna......anya baki fiya son kanki da yawa ba kuwa da wannan birkitaccen hamman naki?" . Murmushi amnan ta saki itama,har qasan ranta taji dadin yadda sabreen ta karba maganganunta,amma har ga Allah tana son matar hammanta ta zama dream wife nashi kaman yadda dukkaninsu suka fahimta "Ki budewa hammana zuciyarki da kyau.....zaki sha mamaki adda.......inajin tukuicin zuwa dubai zakimin duk sati.....nayita zuwa ina ganin burj" Murmushi ta sakeyi kawai batace komai ba......abinda ya bawa amna daman sake cewa "Adda.......na baki kadan daga tarihin hammana dana samu tun kafin a haifeni.....wannan ne kadai zai zame miki jagora wajen sake fahimtar waye.....ya kuma.baki qwarin gwiwan tallafarsa" Zame hannuwanta tayi daga cikin na amna tana girgiza kai "Zaki bani.....amma ba yanzu ba amna.....kinga bana jin dadi sosai" Itama tayi maganar tana narkewa amna kaman yadda amnan keyi. Murmushi ta saki tana tuna warning nata da anni tayi akan ta kula da ita,kuma kada ta matsa mata da yawa,don haka sai tace "Mu barshi pending......har sai kin samu lafiya" Kai ta gyada tana lumshe ido kadan "Na gode" Har qasan zuciyarta tana jin dadin yadda amna ta fahimceta ta qyaleta. Sam bata son jin komai daya shafeshi,saboda tasan zasu fadi kirkinsa ne kawai bawai don haka yake ba,zasu fadi kirkinsa ne don haka yake nuna musu a fuska da mu'amalarsa da su,amma a waje kuwa.....babban azzalumi ne a wajenta mugu kuma. Maida dubanta tayi kan maamah "Ban taba kiran wani d'a namiji da adadi me yawa ba irin wannan sai d'anki......na masa kiran qarshe......inaso naga naki qoqarin" Abinda fareeda ta fada kenan ranta yana motsuwa hadi da qara baci akan lamarin. Bata taba daukan plan dinta bazaiyi wani aiki ba,kudade ta kashe masu nauyi don a buga ninkin adadin news paper din da aka saba bugawa a kowacce rana......sannan a fiddata tituna a kuma rabata kyauta ga kowa basai kowa ya siya news paper ba a ranar. Guri daya maamah ta zubawa idanu tana murza tafin hannunta,tana ji a jikinta lokaci yayi da zata koma wajen boka ta zube masa komai.......ta gaya masa buqatarta ta gaba,ta zube masa ruwan kudin da ko bai shirya ba dole yayi aikin nan......daga can wani loko na zuciyarta tana fargaba.......tana fargabar kalamansa na can watannin baya......kalamansa na qarshe a haduwarsu ta qarshe dashi. _taurarinta nada tsananin haske da wahalar cusa kai a cikinsu.......tabata abune da zai iya zuwa da nasara da kuma akasinta.........KINYI KUSKUREN ZABINTA......amma itace mahadin masarrafin b'arin nasa tauraron..........taurarinta sune abokan tafiyar nasa taurarin.........kusan komai nasu suna kamanceceniya da juna.......ITACE TA DACE DA CIKAR BURINKI MUDDIN AKA SAMU GUSHEWAR AKASIN DA NAKE HANGOWA_ Gumi ne taji yana tsatsatsafo mata......a take sai taji ai kaman ta fara shiga matsalar daya ambata mata. Sai yanzu kwanyarta ta fara aikin da a wancan lokacin bata yishi ba wato na fahimtar ma'anonin maganganunsa. Kenan aikin banza takeyi?,kenan ba wadda zata iya cika mata burinta akan faud sai sabreen din da take kokawar fitarwa a gidan?,wannan wanne AKASI NE da boka ke magana a kai wanda yace muddin ya gushe ita zata iya cika mata burinta......wanne akasi ne?. *_DUNIYATA LITTAFIN KUDI NE(PAID BOOK),KAI TSAYE KI TUNTUBI WANNAN NUMBER_* 08187255862 𝐃 𝐔 𝐍 𝐈 𝐘 𝐀 𝐓 𝐀 _Zafafabiyar_ ̶B̶O̶O̶K ̶2 ⱧɄ₲Ʉ₥₳ 𝙋𝘼𝙂𝙀 66 66 _ko kisan manzan Allah S A W da kansa ya kasance yana neman tsari daga sharrin abinda ya aikata da wanda bai aikata ba? Yakan ce"Allahumma inni a'uzu bika min sharri ma amiltu wamin sharri ma lam a'amal"_ _shi daya kasance Allah ya gafarta masa duk wani abu da zaiyi da wanda ma yayi,ina gake?_ Dukka jikinta sai ya dauki wani irin dumi,tamkar ma ta manta da fareeda dake zaune gefanta,wani yalwataccen tashin hankali ya duro mata......cikin qasa da minti guda taji tana tsananin buqatar ganinsa. "Ke nake sauraro" Muryar fareeda ta yanke mata tunaninta. Idanu ta zubawa fareedan na wasu daqiqu kafin ta kammala tunani a kanta dukka cikin sakanni,murmushi ta sakar mata. "Mu da kikaga muna cimma nasara a rayuwarmu......ba da gaggawa muke tafi da komai ba......kibarmin komai a hannuna......indai kinga baki samu fu'ad ba.....to tabbas bani na haifeshi ba". Maganar ta faranta ran fareeda duk da ta xuba mata kokwanto me yawan gaske. Amma itama ta yarda da kanta......tasan kuma nata kalar takun,don haka ta miqe da nata murmushin tana ajiye mata bundle na dollars. "Ki qara da wannan......amma buqatata yazo ya ganni koda na minti talatinne kacal" Ta furta tana zuge zip din Jakarta,a qasan ranta kuma tana samun tabbacin da gaske ne fu'ad baya sakar mata zallar ruwan kudi.......abu na farko daya fara jefa mata shakka a zuciyarta akan matar. Matashin billionaire irin muhammad jadda......wanda tsananin yawan dukiya da arziqin daya mallaka a gefe guda quruciya da kyau su suka saka mata kwadayin mallakarsa......kudaden data bata din ya kamata ace a kullum a arziqinsa basufi kudin siyan wasu qananun abubuwa ba....amma ya zamana ita ke fara'a da samunsu?. A arziqin mahaifinta idan aka kasa arziqin fu'ad hamsin qwaya daya ne.....amma ace ita karan kanta tana da qarfin halin yin kyauta irin wannan?. TABBAS AKWAI MAGANA.....MAGANGANU MA,ta furta a sarari qasa qasa. Kudin kawai take juyawa a hannunta farinciki yana kamata. Ta samu kudin da zata tunkari aikinta,duk da tana baqincikin yadda kudin xasu salwanta,amma kuma idan ta tuna da ribanya ribarsu da zatayi sai taji koda ta salwantar da finsu ma ba komai bane. Saidai tana buqatar magana da yarinyar.......maganar da zata sake bata haske akan mataki na gaba da zata tabbatarwa boka shi take da buqata. Wa zara kira?zuwaira..... Kira daya biyu uku hudu har goma wayar zuwaira a kashe take. Tayi tsaki har batasan adadinsu ba,da waye zatayi magana ya hadata da yarinyar?. Tsam ta miqe data tuna daxun maganarsu ta qarshe zuwaira ta gaya mata yarinyar taje gidan ita da mamarta,saidai batasan ko tana can ko sun dawo ba. Ta qwalawa badawiyya kira "Ki tafi gidan hamza ki karbomin number wannan yarinyar" "To hajiya" Ta amsa mata a ladabce sannan ta juya tana ficewa ba tare data tsaya jiran komai ba. Hannunsa ya sanya saman labbansa kawai yana sauraren bayanin manager na gidan jarida na qarshe da yakeyi,wanda banbancinsa dana sauran qalilanne "Amma wallahi wallahi ranka ya dade kaman yadda 'yan uwana suka fada ne......wallahi bansan sadda aka buga labarin ba......ni dinma kamarsu gayyata na samu na taron 'yan jarida unexpected.......amma sanda na iso na samu jaridar ta fara fita hannun dealers na dakatar da saidata......waye zaiyi wasa da mutum kamar kai?,wanne gangancinne zai debi mutum......ko baya ga haka kana da mutunci da martabar da bai kamata mu bari a bata sunanka dana iyalinka ta wannan hanyar ba" Mutumin da aqalla ya kusa shekara sittin a duniya ya fada cikin matsanancin takaicin yadda duk karamci irin na jadda jaridarsa ta shiga sahun wadanda suka ci masa mutunci....duk da Allah ya taqaita an daqile fitar jaridar. Iska me zafi ya furzar daga bakinsa yana sauke qafafunsa qasa,kanshi yana sake daukan zafi da lamarin. "Inason list na dukka mutanen dake da aiki a ranar a dakin buga labarai.......da full details na kowa" Ya fadi a ransa yana jin zaiyi aikin daya jima baiyi ba. "Sir.......ai mun kammala wannan.....muna jira ne kawai ka gama ji daga bakinsu......dukkanin dealers din mun karbi copy na newspapers din daga hannunsu,yanzu haka ba wanda keda sample nata.....Allah yasa munyi abun da sauri basukai ga rarrabawa qananun 'yan kasuwa ba,mun samu dukkanin jerin mutane hamsin da uku dake da aiki ranar a gidajen jaridu ukun......saidai mun rasa mutane uku a ciki,mutum daya daga gidan kowacce jarida......abinda ya qarfafa zarginmu akan suke da hannu.......na tura ma'aikata don binciken inda suke,kuma ina saka ran koda wanne lokaci zasu bani information,amma sauran mun tabbatar basu da masaniya akan komai" Wani abune daya tsaya masa tun jiya ya dinga sulalewa yana narke masa,ya gyada kai yana jin sassaucin dunqulallen abun daya tare masa wuya. Kafin yayi magana aka nemi izinin shigowa dakin. Ma'aikacin ya duba ya kuma bada izinin shigowa. Salute nasa sukayi mutum biyun da suka shigo,suka kuma miqa masa wani takardu. "Auwal sadi.....nura mahadi......labaran isyaku.....gaba dayansu mun samu tabbacin sun fita daga qasar nan kusan awanni biyu da suka shude,saidai kowannensu mun samu tabbacin qasar daya sauka.....auwal ya sauka a uk.......nura South Korea......shi kuma labaran ya sauka a china". "South korea.....UK.....china" Fu'ad ya furta sunayen a fili yana irgawa da yatsunsa,sai ya fesar da iska a bakinsa yana maida dubansa kan CP. "Well done sir......i really appreciate your effort,thank you for your hard work.......a sallamesu inason muyi magana privately" "Okay sir" Ya amsa masa cikin girmamawa. Cikin qasa da mintuna ya sallami kowa,ya kuma riski fu'ad din cikin motarsa qirar Mercedes sprinter. Duk yadda yaso mazewa da ganin alatun dake cikin motar tamkar kana cikin wani hamshaqin parlor din bawai mota ba amma ya gaza,sai daya daga kanshi ya kalli saman roofing din da yafi kama da lafiyayyen roofing din dakin sanda fu'ad ke qara hasken cikin motar daga galaxy blue stars zuwa brighter light. "Ina expecting tafiya nan da kwanaki uku......inason kayi gaba da kula da komai har zuwa sanda zan dawo......saidai banason binciken ya dakata......zanyi qoqarin ganin an kawosu daga dukka qasashen da suka tsallaka din don su fadi wanda ya basu contract din......wadancan mutum biyun kuma,ko tambayarsu bana fata kuyi.....ajiya na baku......irin ajiyar nan ta ma'anan ajiya" Yakai qarshen maganar yana tura cheque na kudi daya rubuta masa masu yawan gaske. Kai ya girgiza "Nop sir.....bazan amshi komai ba,aikina ne nakeyi kuma dole mutum irinka a masa aikin daya dace saboda alfanunsa ga al'umma". Wani abu dake gefansa ya dannan wata qaramar ma'ajiya ta fito,ya jefa cheque din yana cewa "Ba bribing naka nakeyi ba.......wannan din kyauta ne na baka,na jima da sanin wanene kai......inda baka cancanata ba ko qwandalata ba zata shiga hannunka ba.....kana daya daga cikin mutane masu aiki tuquru da qoqarin kamanta gaskiya duk da yadda qasarmu ta lalace.....so you deserve it,xan baka koda bakamin aikin komai ba" "Thank you sir.....thank you so much" S.nuhu ya fada yana jin dadin gwaggwabar kyautar da me jadda din ya bashi. Tunda wuri taqi zaman parlor din don batason ma ya dawo shi ya gansu ko ita ta ganshi,ta zame tayi zamanta a daki dole amna ma ta biyo ta can. Tana saman sofa din dake gefe daya a dakin,amna na zaune saman tattausan carpet din tana assignment. Idanunta kan takardun tana jin sha'awar amna din,tana jin inama ace itace ta samu dama irinta amna?,inama ace ta samu daman zuzzurfan karatu kaman amna?,wadda gata ya sanya tace bazatayi karatu wata qasar ba tsabar samun dama. Maida bangon littafin tayi tana duban sabreen cikin murmushi "Done......sai yanzu hankalina ya kwanta...lecturer dinnan mugu ne adda.....any mistake game over" Murmushi ta tayata dashi,ta jawo jakarta tana qoqarin maida litattafan "Adda......kin taba jin labarin labarin uwar data watsar da yaranta tun suna qananu ba tare data damu da waye zai kula dasu ba?,waye zai zama gatansu?" Takai qarshen maganar tana zuba idonta akan fuskar sabreen. Maganar sai tayi ma sabreen wani iri,a hankali ta girgiza kanta "Aah amna" "Kin taba jin labari,bayan wasu shekaru ta dawo garesu,amma kinsan me yasanya ta dawo garesu?" Kai sabreen ta sake girgizawa "Kudi......arziqi da rufin asirin da suka samu tazo ci,ba yadda suka rayu bane damuwarta......ba lafiyarsu ko akasinta ba". Idanu sabreen ta zubawa amna tana jin labarin ya kasa kama hankalinta,tsahon wasu mintina ba wanda yace da kowa komai,har sai da sabreen ta fara magana "Wanne irin cukurkudadden labari ne wannan amna?,a ina kika jiyoshi." Qaramar dariya amna ta saki tana janye jakarta gefe "Labarin mijinki kenan.....hamma na....." Bata qarasa ba shigowar saqo wayarta ya katse sauran maganar dake bakinta. Wani irin shuru sabreen tayi lokacin da hankalin amna yayi kan wayarta "Maamah?,mariya?....." Abinda kawai sabreen ke iya juyawa cikin ranta kenan "Bai rayu da ita ba?......batasan komai nasu ba?......batasan wahalarsu ba?,dukiyarsu tasa ta dawo??,dukiya???" Tarin tambayoyin da suka jujjuyawa cikin kwanyarta kenan. Maganganun amna gaba daya sai suka kasance mata kamar ta jefeta da wata cukurkudaddiyar sarqa,ta kasa hada daya da daya ya bata biyu. "Unbleavable!......oh my god!" Amna ta furta da wani irin qaraji,abinda ya yanke zaren tunanin sabreen kenan,ko kafin ta farga har amna ta fado jikinta ta cukuikuyeta "From nigeria to Maldives........wedding bells adda.......wedding bells" Ta fada tana dariyar dake cakude da farinciki zalla a muryarta. Qoqarin dagata sabreen takeyi cikin murmushi da mamakin abinda ya sanyata tsananin farinciki irin haka "Zaki karyani auta" Ta fada a dan shagwabe tana riqe amna din. Da sauri ta dagata tana fadin "Am sorry adda.....wani irin mamaki uncle BB ya bani......yayi surprising dina irin wanda ya jima baimin ba......adda hutunmu na wannan shekarar zai fara daga Maldives......kinsan mafarkaina akan wajen kuwa?,kowanne year idan anzo zaben wanne qasa za'a je idan na kawo sai BB da saddiq sun kushemin.......yaa musaddiq kawai ke goyon baya na" Ta qarasa maganar muryarta a narke,da alama tana jin haushin yadda abun yake kasancewa. Dan murmushi sabreen ta saki,don ita inda take maganar ma batasan ina bane ballantana tasan muhimmancin da yake dashi ba da za'a dokanta aje. "Your dream have come true" "Really adda.......adda wannan shine tafiyan da zatafimin kowacce dadi da alama......ina da sister like you nima wannan karan.......ha saddiq ya daina yimin gori idan za'a fita......i don't know yadda zan miki bayanin Maldives......but gani ya kori ji" Dan qaramin murmushi ta aje mata kawai don ita bataga wani abun doki ba a nan. "Labari na biyu adda.....muna da biki,borno zatayi kira......bikin BB farouq date din yayi daidai da dawowarmu da sati biyu kacal". "Ma sha Allah.....Allah ya sanya alkhairi" "Wannan qarshen shekaran bame sauqi bace adda......can't wait......bari na bawa besty labari" Ta fadi tana laluben number wayar aminiyarta guda daya da take da ita. "Adda......anya ba honeymoon BB farouq ya hada muku keda hamma ba?" Amna ta dakata daga qoqarin kiran besty din nata da take tana duban sabreen. Bata jira ma sabreen ta bata amsa ba ta saki dan qaramin ihu tana tsalle gefe "It makes sense👌.....that's my big bro farouq" Amna ta fada tana dariya nishadi kaman zai kasheta. Baki kawai sabreen ta kama tana kallon amna "Amna......nace miki binku zanyi?". Tana dariya ta bata amsa " It's for the whole family adda........kowa ma yana tafiya hutu a wannan lokacin,indai kai under jadda family kake......hatta ma'aikatan dake aiki cikin gida lokacin hutunsu ne.....kawai dai,nayi mamakin rage date din da aka saba tafiyan" Ta fada tana duba wayarta. Rasa abinda sabreen zata fada tayi,maganan gaskiya ita sam bata shirya zuwa ko ina dasu ba,don bata jin tana cikin family dinsu,hasalima tazara take son bayarwa tsakaninsu. Duk sanda amna ke waya da qawarta ita tayi nisa wajen juya maganganun amnan. Wani irin mamaki ke tsarga mata,wai dama haka matar take tun usul?,ta yaya zata samu gaskiyan abinda amna ta gaya mata?,tun tale tale gurbataccen hali gareta?,indai haka ne mene yaran sukayi me muni da zata cutar dasu?. Kwanyarta ta sake harbawa,da qarfi da yaji ta soma qoqarin hada daya da biyu ko zata bata daidai *_DUNIYATA LITTAFIN KUDI NE(PAID BOOK),KAI TSAYE KI TUNTUBI WANNAN NUMBER_* 08187255862 67 _Manzan Allah S A W yace "idan dayanku zaiyi fada/zai daki dan uwansa,to ya guji fuska/kada ya mari fuskarsa_ 🧏🏽 _sai a kiyaye,mari ko dukan fuska haramunne a musulunci_ "Biri yayi kama da mutum,tsananin qaunarta da duniya da kuma dukiya,shine silar qoqarin mallakar d'anta ta qarfi da yaji?,wannan shine daliinta?". Numfashi ta fitar me nauyi tana saka hannuwanta saman fuskarta " Adda......maamah keson magana dake" Amna da sunan maamah din ya fito ta true call din ya gaya mata wace ta fada kai tsaye,duk da bata da tabbacin da sabreen takeson magana. Hannu kawai ta bawa amna,tana maida wayar kunnenta. "Har yanzu kina kan bakanki?,kinci gaba da lamuntar jefa rayuwarki cikin hatsari maimakon tseratar da rayuwar taki?,a naki tsammanin kin tsira kin tseratar da yan uwanki?" "Idan kura tana maganin zawo ta yiwa kanta mana?". Dif maamah tayi,batayi gaggawar amsa mata ba,don maganar ta jefeta da wani qudundunanniyar ma'ana. "Kece kike sake tafka kuskure akan kuskure......kuma kwanaki dukka wani sirrinki yana qarewa.......komai yana dab da bakaduwa tamkar yadda iska ke diban lallausan gari tana watsashi cikin mutane........ashe ba kaina kika fara nuna rashin sanin darajar halittar D'A ba......ashe baiwa ce sanin darajar haihuwa a zuciyar iyaye......d'anki bashi da muhalli ko daya a zuciyata ko rayuwata,.....kaman yadda banda sha'awar zaman aure dashi......saidai fita a gidansa da rayuwarsa duka sai sanda naga dama... Kinsan yaushe nake nufi?" Bummm zuciyar maamah ta buga tun bataji qarshen zancen ba "Zan fita ne a sanda na gama karanta masa ainihin WACCE KALAR UWA yake da ita......ba don ina sonsa ba......sai don alkhairi guda daya tak da yayimin........ya karbo 'yan uwana daga hannunki ya kawominsu......abinda yayi silar takawarsu tudun muntsira......ya sanyasu hayewa duk wasu qananun qullinki.....zan saka masa da iya wannan,don bashi da wata nagarta ko guda daya da zata sanya sabreen sha'awar kasancewa dashi......ki riqe wannan......ki rubuta ki ajiye......sabreen ce zata zame miki silar BANKADA!" Tana kaiwa nan saita kashe wayar ta azata saman cinyarta tana ci gaba da lullube fuskarta "Ya hayyu ya qayyumu bi rahmatika astagis" Ta dinga maimaitawa,tsanar uwa da danta duka suna turereniya cikin zuciyarta. Ko da amna ta dawo abinci kawai taci ta fara list na abubuwan da zasu buqata lokacin tafiyar da abinda zasuje dashi. Ba wani abu data tofawa amna sai idanu da take binta dashi. Ba qaramin jarumta tayi ba da take iya binta da murmushi ba,gaba daya ganin abun take a wani abu maras yuwuwa,ita ba ahalinsu bace,bata kuma tunanin zata zama ahalin nasu.....hasalima gaba daya lissafinta yafi karkata ga qarawarta gaba kafin sukai ga dawowa daga yawon qasashe hudun da suka tsara zasuyi,kowacce qasa zaman sati guda zasuyi,ciki kuwa harda umra data zame musu dole duk lokaci irin wannan. Dukka maganganun sabreen sukayi mata tsaye a rai,a daren ranar duk inda ta juya furucinta ne ke mata kai kawo a rai. Tanaso jin rauni game da yarinyar yana sauko mata,amma wannan dakakkiyar zuciyar da shedaninta dake gefe suna gaya mata _karamar halitta irin ta mace......yarinya qarama me qananun shekaru bai kamata taga rauninki ba.....bai kamata ace itace taci galaba samanki ba_. Abu daya ta kasa samun aminci akan yarinyar shine 'Yiwuwar aikata komai". Ko ba'a fada ba ta sani......sabreen zata iya aikata komai,tana da taurin zuciya da qwarin zuciya dama zarrar da zata iya yin komai.....wannan zarrar tata ita taja hankalinta ta zabota zuwa ga aikin da bata taba kawo komai zai warware da wata irin faduwa da rashin nasara haka ba. Tunda ta idar da sallar asuba bata koma bacci ba. Ta jira har sanda gari yasha,sannan tayi wanka,ta shirya kaman kullum da qasaitattar shigar nan tata dake qara mata jin izza da jin takai inda ya kamata ace takai din,saidai bata qarasa gabar da take da muradin qarasawa ba. Wayarta ta fitar ta kira driver dinta,ya tabbatar mata yanzu haka yana cikin mota yana jiranta,kai tsaye ta dauki jakarta tana yafa mayafinta ta fice. Dab da zata bar falon taji laila na kiranta "Maamah" Tsaiwa tayi tana jan tsaki,don bata shirya komai ya dakatar da ita ba. Qarasowa lailan tayi,ta kuma zube a gaban maamah din. Sam tun daga waccan ranar bata iya tsaiwa gaban maamah.....magana ce ko gaisuwa zubewa takeyi a gabanta tamkar bawa da uban gidansa. "Ina fatan ba wani abu nayi miki ba maamah?" Ta tambaya da tsananin tsoron kada ranta ya baci "Naga zaki fita baki tasoni ko kisa an gayamin ba" . Wani qaramin tsaki maamah din ta saki,wannan abun ya fara isarta,ba wani motsi da zatayi sai yarinyar ta buwayeta. Irin wannan abun da akan fu'ad ya fada tabbas zata iya cewa tafi kowanne mutum sa'ar zuwa duniya. Ko yaya taga fuskarta ta canza takanyi kaman zata fashe da kuka,komai kuma har abinda bai dace ta sani ba game da lailan lailan saita gaya mata "Unguwa zanje,kafin na dawo ki gyara falo din,ki hada da bedroom din,duk abinda kika gani ki ajiyeminshi inda kika ganshi,kada kibar kowa ya hauramin sama,akwai underwears dina dana cire ki wankesu ki shanya a backyard ki jira su bushe ki dawo min dasu ciki" "In sha Allah an gama,Allah ya dawo dake lafiya" "Amin" Ta amsa tana yin gaba. Sau tari idan taso bautar da laila sama da haka sai wata zuciyar ta gaya mata lailan kome tayi bisa jagorancin mahaifiyarta ne,wannan ya sanya take sassauta mata akan abubuwa da dama. Tafiyar awa daya da rabi cif suka fara gangarawa mummunan jejin,sai da suka sake kashe wata awar sannan suka isa. Daga nesa ta sanya driver din ya sauketa,sannan ta tattare zanin tsadaddar atamfar jikinta ta fara tsallake qayoyi da busassun tsirrai tana wucewa ciki. Gurine da zaiyi wahala kaje ka taras d wani duk da tarin al'ummar dake zuwa wajen a kulli yaumin neman duniya,tamkar sun manta da wata rana da zaa shimfidesu babu wannan ruhin daya zama masarrafi na motsinsu da kai kawonsu izuwa gurare daban daban. Ba wata kafa a jikinta da bata fitar da gumi sanda take zaune a gabansa tana jiran bayanansa na qarshe. Da qyar ta samu ya ganta.....don sharadinsa ne baya aiki biyu akan matsala guda daya. "ZANGON NASARAKI guda daya ya rage miki......BANKADA zata sameki.....tonon asirinki zai fara daga yanzu zuwa kowanne lokaci.....zangon nasararki zai iya narkewa ya dulmiya sanadin hakan!!!" Ya furta da wata irin murya maras dadin amo. Dukkanin 'ya'yan hanjinta taji sun tattara sun cure guri daya,idanunta suka qara girma saboda wani sabon kalar tashin hankali da bata taba jin makamancinsa ba "Kanaso kacemin itace zatayi nasara a kaina?!!!" "Me muka gaya miki wancan karon?!!!!......" Wasu muryoyi da tafi tsammanin sun kusa guda goma sukayi amsa kuwa a wajen kafin bokan ya karba "KINYI GANGANCIN ZABOTA......SAIDAI TAURARONSA DA NATA TAURARIN KADAI SUKA DACE......ITACE KADAI MAHADIN AIKINKI........zabi biyu gareki.....ko ki kasheta duk wani burinki ya dulmiya ya koma mafarki......ko ki barta ta rayu kina kallonta kuma naki burin shima yana raye amma babu wata dama ko hanyar cikashi.....zan miki wani aiki guda daya......amma daga kansa!....ina me gargadinki kada ki kuskura ki sake dawomin akan matsalar data shafesu.......aiki yayi kyau ko akasin haka......". "Na gode da wannan dama daka bani.....na tare dakai su dafa maka" Ta fada jikinta yana rawa da jin qarin dama guda daya,abinda a tarihinsa bai taba ba maimaicen aiki. "Zaayiwa na tare dani da ma'aikata yanka......zasusha jini wadatacce da zasuyi aikin jinkirtawar tonuwar asirinki........yayin da zangon nasararki ya kama......nan da kwanaki goma sha hudu zuwa ashirin da daya......kiyi duk abinda zakiyi wajen ganin muradinki ya cika......ke zaki yiwa kanki wannan aikin.....mun miki alfarmar samun jinkiri kadai.....amma ki sani tabbas RANAR HASARA DA RANAR TABEWA TANA NAN ZUWA.......DOLE KI FUSKANCETA DA DUKKANIN ZUNUBANKI.........KIYI NESA NESA DA MATSANTAWA TAURARINTA........BA NASARA TA KUSA KO TA NESA......NATA ZANGON NASARAR YANA DAB DA FADOWA HANNUNTA". Duka bayanansa bai wani dameta ba......zangon nasararta da damarta guda daya daya tabbatar mata ita tafi komai yi mata dadi. Kudade masu kaurin da suka haura million hudu ta zube masa,sannan ta fita da baya da takalmanta a hannu ranta fes,tana gayawa kanta dogon zangon tunani ya zame mata dole don samun kyakkyawar mafita. Tabbas ta kowacce fuska tana da buqatar barin sabreen gidan koda itace murfin nasararta.......gwara tasan yadda zatayi ta maye fareeda da ita a madadin cikar burinta. ★Hadith yana daya daga cikin karatuttukan da suke mata dadi qwarai. Sau tari idan suna karatunsa da rumaisa yafi kowanne littafi daukan musu lokaci. Ko a yanzun da take zaune tana bita amna na zaune a gefanta,sunata hira da anni wanda rabinta kusan na tafiyarsu ce jibi,lokaci lokaci kuma da tsare tsaren abinda zaa gudanar da bikin farouq. "Anni....gata karatu take,ki mata magana don Allah" Ta fada a narke. Duk da sabreen batasan akan me amna ke magana ba,amma sai data daga kanta da sauri. Tana balain jin kwarjinin matar da ganin kimarta,daidai nan amnan ta miqo mata wayar tana danne dariyarta hadi da hade hannun alamun am sorry. Da idanu ta nuna mata zan kamaki sannna ta karbi wayar tana sakawa a kunne "Barka da dare d'iyata.....ina fatan dai bata miki shirme?" "Barka da dare anni....." Ta fada tana murmushi "Ya jikin naki?...ina fata dai kinji sauqi?" "Alhmdlh na warware....anni na gode" "Ba godiya ai tsakanin uwa da d'iyarta......nace ba,nasan halin yarona sarai,duk sanda tafiya irin haka ta kama saidai a tayashi shirya kayanshi shi kansa,nace idan akwai wani abu da kuke buqata na tafiyar kiyi magana....karki daukeni suruka ameenatu ni mamarki ce,ki rubuta sai a kawo,idan kuma ta amnan zakiyi to saiku fita tare goben,saiki masa magana" Kunya ta sake kamata,bangare daya kuma tana jin wani iri. Ta aza an soke zancan tafiya da ita ne kwata kwata,don tun randa akayi maganar da amnan tace BB farouq yace ta bada details dinta da sauransu bata sakejin komai akai ba. "In sha Allah anni......Allah ya saka da alkhairi ya qara girma" "Ameen ameen,a baya magaji ne yake hada masa necessary abubuwan da zai tafiyar dasu.....ina fata yanzun zaki maye gurbin hakan?" "In sha Allah" Ta amsawa annin tana jin wani qaton nauyi ta aza mata akai,daga nan ta miqawa amna wayar ta maida kanta kan karatun. Amma kuma sai karatun ya gagareta,saboda batasan yadda zata cika maganar anni ba. Batason haduwa dashi kwata kwata,hakanan idan batayi yadda annin tace ba zai zama kaman rainuwa,kuma amna da akayi a gabanta ba zataji dadi ba. Dabara ce ta fado mata,ta rufe littafin tana duban amna data gama wayar. "Kina da number magaji din?" "Eh ina da" Amna ta amsa mata "Faka faka kiramin shi" Ta furta tana gyara daurin dankwalinta. Sosai abun ya yiwa amna dadi,ta kira magajin ta hadata dashi. "So nake nasan da meye da meye ake hadama boss idan zaiyi tafiya?". Tayi maganar tana miqawa amna hannu alamun ta bata takarda da abun rubutu. A ladabce ya dinga zayyano mata tana rubutawa,har ta gama tsaf tayi masa godiya ta yanke kiran,ta miqawa amna bironta ita kuma ta miqe da takardar a hannunta,amna ta bita da kallo tana murmushi. Tasan abinda take shirin yi,zataje ta hada masa jaka tana tunanin baya nan kafin ya dawo,saidai tun daxun taga shigowarsa,kawai bata gaya mata bane tunda ta lura ba hawa saman take ba,itadai adduarta daya Allah yasa adda sabreen din bata cikin sahun shashashun matan nan da basu iya baiwa miji kulawa,duk da itadai a hakanta a halittarta bataga alamun hakan ba. Duk da tana da yaqinin baya nan,amma duk taku daya sai bugun zuciyarta ya qaru,kaman yadda numfashinta ke fita da nauyi. Bude smart door dinsa bame wahala bane a wajenta,saboda tuntuni ya sanyata cikin sahun masu shiga kai tsaye. Ko ina fes kaman yadda ta saba,yana fita da safe take shiga,tasan lokacin fitarsa,zai kuma wahala ya wuce wannan time din be fita ba,zata shiga ta kintsa komai. Duk da baya barin komai sai dan goge goge da qananun datti,bai taba barin underwears dinsa ba koda kuwa singlet nashi bata taba gani ba,abinda ma ya sanya mata qaramar nutsuwa kenan. Bedroom dinsa ta wuce,tayi kuma amfani da details din da magaji ya bata ta dinga fiddo da komai,sai data hada shi tsaf sannan ta rufe briefcase da luggage din ta ajiyesu a gurbin da ta tabbatar zai wahala ya kasa ganinsa. Yadda batayi zaton ganinsa ba haka shima baiyi wannan zaton ba. Batasan ya shigo saman ba kwata kwata. Ta zare idanunta daga cikin nasa idanun da yau take ganin kamar sun rusuna sunyi kuma laushi,can qasan ranta tana mamakin yadda ya balbalawa kansa A.c tayi qau a falon,abinda iya saninta dashi ba sabonshi bace. Idan kaga ya kunnata ma to tabbas ranan ana zafi,ko kuma bai samu irin fresh air din da yakeso ba. Kanta ta dauke sosai ta fara takawa zata wuceshi,yau daya sai taji tana jin shakkar giftashi,koda kuma bata kalleshi ba tana jin kaman idanunsa a kanta suke. Allah ne kadai ya sauko da ita,don bibbiyu bibbiyu take hada stairs din tana saukowa,tana jin kamar zai biyota yayi jan masifar daya saba,tana kawowa bakin bedroom dinta ta saki numfashi tana danne qirjinta. Sai data bacewa ganinsa ya dauke kansa daga wajen yana maida hankalinsa kan wayar huda dake hannunsa wadda yakewa kallon wayarta. Tun ranar yake sake zurfafa bincike cikin wayar......amma kullum abinda zai gani a ciki taba masa rai yakeyi. Tarin massages na nuna zallar soyayya da kewa,zuciyarsa ba irin abinda bata raya masa yayi ba amma yana danneta d wani irin qarfi dashi kansa baisan yana da ita ba. Abu daya ke taka masa burki,cases din da zaiyi tafiya ya bari,amma ya tabbatar zuwa sanda zai dawo komai yayi settling......a lokacin zata kwashi kashinta a hannu,zaikaita ainihin kurkukun da itace asalin wadda ya tanadar mata. Qarar wayarsa ya janye hankalinsa daga wancan tunanin,ya dauka yana dubawa don kusan duka saqon da zai shigo masa me amfani ne. _ko a kusa ko a nesa duk inda zaka ina tare da kai,toshe kirana bawai yana nufin toshe soyayyarka daga zuciyata bane........ferree dinka ce_ ta saka sign na kiss da love daga qasa Matse wayar yayi a hannunsa,yanajin bai taba jin tsanar wani abu a duniya ba irin yarinyar......tabbas tace zataci gaba da bibiyarsa nan da sati daya zai nema mahaifinta yayi magana dashi. Y janye diyarsa ya siya mata girman da ita ta gaza siyawa kanta. ★A daren washegari zai shigo mata amna tayi kawai da wata irin luggage da itadai idan tace ta taba ganin akwatin daya mata kyau irin wannan tayi qarya. Komai da matafiyi zai buqata an kammala mata shi an damqa mata a hannu. Wayar amna ta karba tayi kiran titi bayan ta zuba numbers din titin data rubuta ta aje saboda gudun bacewa. Har yanzu tana mamakin yadda wayar huda ta sake bacewa a dakin,saidai zuciyarta tanata qarfafa mata zargin shine ya sake daukewa.......don tun randa wancan incident din ya faru bata sake ganinta ba. Magana sosai sukayi da titi din dasu huda,ta kira momma bahijja ma ta mata sallama,hankalinta ya kwanta sosai data samu yaqinin cewa kwana uku da tafiyarsu suma zasu isa mali,kunya tadan kamata sanda momma din ke tsokanarta honeymoon zasuje? "Saura satittika kadan ya rage nima na biyo bayansu zuwa tushen mahaifiyata momma" Ta furta a ranta. Sosai taji zuciyarta sakayau,hankalinta ya sake kwanciya,amma saita dinga jinta cikin wani kadaici,tana jin kamar ita daya tayi saura a Nigeria,saidai kuma tana jin sassauci idan ta tuna itadinma kwanaki kadan zata iskesu su sake shimfida sabuwar rayuwa me inganci tare. _hmmmm,nace ko dama zata bada daman hakan?_ *_MALDIVES........_* *KOMAI NISAN JIFA*👇🏾👇🏾👇🏾👇🏾👇🏾👇🏾 *_DUNIYATA LITTAFIN KUDI NE(PAID BOOK),KAI TSAYE KI TUNTUBI WANNAN NUMBER_* 08187255862 68 *_Na muku post saboda jiran kwana biyu da kukayi,don Allah banason complain,dole zaa zo inda kuketa zakwadin🧏🏽🤦🏽‍♀️🙄_ _Allah don isar mulkinka,don buwayarka,don girman soyayyar da take tsakaninka da muhammadurrasulillahi,dukkaninmu bayinka ne,amma akwai bayinka dake zaluntarmu suna fitar mana da pages,Allah kafi kowa sanin yadda muke wahala,mun killace haqqinmu bamu tilastawa kowa ba akan yazo inda yake,amma suna biyomu suna zaluntarmu YA ARHAMAR RAHIMEEN KAFI KOWA SANIN BAMU ZALUNCESU BA....YA ALLAH KO WACECE IDAN BATA DAINA BA ALLAH MUN GATA NAN,MUN KAWO QARARTA KOTUNKA ME ADALCI,YA ALLAH....YADDA TAKE TARWATSA MANA KASUWANCI UBANGIJIN SAMMAI DA QASSAI KA TARWATSA NATA KASUWANCIN,ASARAR DA TAKE JA MANA ALLAH KA NINNINKA MATA WANNAN ASARAR AKAN NATA KASUWANCIN DON ISAR MUHAMMADUR RASULILLAHI A FADARKA AMEEN_ *_REPUBLIC OF MALDIVES_* *MALÉ* *Velana international airport malé_* Misalin qarfe hudu agogon Maldives wanda yayi daidai da qarfe takwas na dare agogon Nigeria private jet din mallakin Muhammad fu'ad jadda wanda ke dauke da sunan JADDA WINGS ya sauka a babban filin tashi da saukan jiragen sama na velana international airport dake babban birnin Maldives wato malé. Daidai sanda jirgin ya kammala tsaiwa gaba daya sabreen ta sauke numfashi a hankali tana lumshe idanunta gami da budesu kusan lokaci daya. Wani abune da take ganinsa tamkar cikin mafarkanta,gata cikin qasar da koda sunanta sai lokuta d'aid'aiku ta taba jinta ballantana mafarkinta yakai ga zuwa qasar. Tun daga kano zuwa lagos da suka sauka na wasu mintuna,kafin daga bisani jirginsu ya taso zuwa Maldives tasan tabbas duniya cike take da yalwa da fadi. Abu guda daya daya dinga bata sha'awa.....wanda ita kanta batasan abun na burgeta ba,sai data samu kanta tana fatan "Allah yasa nan gaba kadan rayuwarmu ta kasance kaman haka....ni huda nadra haneefa". Bawai kalan arziqin jadda family bane abinda yaja hankalinta da gasken gaske ba....a'ah.....kalar qaunar juna.....bawa juna kulawa da kuma soyayyan juna da take gani a idanunsu irin na zallar 'yan uwantaka. A tsakaninsu zata iya cewa ta zama 'yar kallo kome daukan rahoto,duk kuwa da cewa sunata qoqarin jefota cikin hirarrakinsu da kowacce magana data shafesu. Sau tari saidai ta murmusa kawai,tana karance da halayen kusan kowa a cikinsu. Farouq nada tsananin kirki......yana da nuna kulawa da soyayya da 'yan uwansa,yana da wasa da dariya da 'yan uwansa.....amma mugun muskili ne kuma hutsu idan baiga dama ba. Saddiq yana da zuciya,yana da saurin fushi amma kuma yana da saurin saukowa,yana da kula da damuwa qwarai da gaske da al'amarin 'yan uwansa. Musaddiq dataji sunata waya dashi kafin tashin jirginsu,wanda a yanzu haka shi yayi landing ma a Maldives din,bazatace ga hali ko dabi'arsa ba,illa abu guda daya data lura. Shima me yawan nuna kulawa ga 'yan uwansa ne da damuwa dasu. Sai oga boss muhammad fu'ad jadda.........shi kadai halinsa yasha banban ta kowacce fuska da 'yan uwansa......ta fuska daya sukayi musharakar halaye,wato ta fannin qauna ga 'yan uwansa......wata irin qauna da a fuska ba zaka ganta ba,hakanan a fili ba zakaga wani alamun damuwa ko kulawa da lamarin kowa bama tattare dashi,saidai kuma yana ankare da motsin kowa da kai kawonsu. Wani irin bahagon miskili da koda magana zaiyi saika rantse ya lissafe take,bayason lafuzansa kuma su qare,kaman tattalinsu yake,baya magana ya maimaita maka,kaman yadda bai fiya nuna damuwa ko zafafawa akan al'amura ba. Zaka dauka bai damu da komai ba,baya kuma kula da komai,saidai kaifin lurarsa akan komai tasha banban data kowa. Yana da wani irin fahimtar komai da kowanne motsi dake kewaye dashi,yana da kaifin lissafi,dogon tsinkaye da nazari kafin yayi magana. Ba'a kan komai kakeji yayi magana ba,ba kowanne abu bane zai kalla yace wani abu ba koda yana sane da wannan abun. Dukkaninsu sunyi tarayya akan abu guda wato son anni......kowa a cikinsu wani unique love yake nunawa annin da qauna me tsananin yawa......takan shiga lissafi me zurfi idan maamah ta fado ranta,amma kuma idan ta tara da 'yan maganganun da amna ta fara yi mata,sai taga lallai komai yana da nasaba da wannan. Ko yanzun ma da jirgin ya tsaya,saddiq nata fiddo musu luggage dinsu daga overhead compartment jordan na sauka dasu,shi kam sai a sannan ya rufe system dinsa da batasan abinda yakeyi ba a ciki tunda jirgi ya daga. Tun zamansu daga lagos har kawo yanzu tana gabanshi. Tana jin farouq daya gaji da yadda ya bata hankalinsa yace "Yallabai hutu fa zamu tafi,tun yanzu ka fara bata tsarin hutun?,ya kamata komai a ajjiyeshi a side ko?". Kai ya girgiza,kaman bazaiyi magana ba,sai daga baya ya daga idanunsa ya zubewa farouq dinsu "Ba zaka gane ba.......koda na tafi hutu bazai yiwu har ta internet na tafi offline ba" Baki farouq ya tabe yana jinjina kansa,can qasan zuciyarsa shi yasan me yake tsarawa. Jordan ne ya qarasa ya tattare masa dukka tarkacensa,yayin da shi kuma ya miqe yana zube hannuwansa cikin aljihun 3pices suit din jikinsa yana takawa gaban anni. Duqawa gabanta yayi kadan yana gyara mata zaman takalmanta da take qoqarin sakawa. "Ina fatan zaman jirgi bai saka ciwon qafarki ya tashi ba?" Murmushi ta saki,tana fatan yadda yake da tsananin kulawa a kanta taga yana yin sama da haka akan matarsa. "Alhmdlh......last checkup din da mukaje ai sun bada dokoki,kuma na kiyaye alhmdlh......je ka duba matarka" Ta fadi tana miqewa hadi da ambaton bismillah. A kunnen sabreen anni ta furta hakan,numfashinta yadan tsaya na wucin gadi,ta danyo rolling idanunta tana miqewa. Batason kowanne abu da zai hadata dashi ballantana ya gasa mata magana. Maganan daya gaya mata kafin tasowarsu daga lagos kadai ya isheta basai ya qara mata da wani ba. Cikin ma'aikatan airport dinne,wani a cikinsu yaketa haba haba dasu ita da amna. Itakam bata kawo komai cikin ranta ba,don bata ma sake masa ba,amna ce kawai ke dan amsa tambayoyinsa,har zuwa sanda zasu wuce sai yace "You look so familiar madam....." Ya fada yana dubanta da murmushi. A dan mamakance ta waiwaya tana dubansa,kafin kuma tace komai ya sake fadin. "A abuja......hotel din....." "Stop mr man!" Dakakkiyar muryar fu'ad ta dakatar da mutumin cikin kaduwar hanji. Sam baiga isowarsa wajen ba,mutumin tun dazu yake masa kwarjini. Duqar da kansa yayi da sauri cikin rawar jiki yana cewa "Sorry sir". Bai ko kulashi ba ya kalli amna,da idanu yayi mata sign na ta wuce,sai tayi qasa da kanta tana yin gaba. Ganin amna ta wuce itama saita taka zata bita,bai hanata ba,yabi bayanta shima,saidai ya gasa mata maganar da sai da qwalla ta diga ta samu sassauci "Shi abun qwarai da mummuna tabo gareshi......mu'amala da tarin mazaje ba shine mutuntaka ba ta d'iya mace.... Mutuncinta namiji daya da zai amsa sunan mijinta,bariki bata da riba kota rana daya ce kuwa......duk wanda zai hada zuri'a da macen bariki saiya shirya......ba qaramin cutarwa bace ga 'ya'yan da zasu haifa idan aka ture nashi matsalan na qashin kansa". "Macen bariki......mu'amala da tarin mazaje" Wadannan kalmomin su sukafi komai tsaye mata a rai. Wanne irin mummunan kallo yakeyi mata ne wai har haka?,wanne mummunan fassara yake mata ne?. Tana ji ta soma gajiya,ta fara kaiwa iyaka,daga yanzu zuwa kowanne lokaci zata iya fashe masa.......ba zata iya ci gaba da dauka ko jurar irin wadannan tuhume tuhumen da maganganunsa da basu da tushe ba,tana jin zuciyarta da idanunta na mata wani irin suya,bata samu sassauci ba sai bayan da jirginsu ya doshi Maldives......hirarrakin family din da uwa me goya marayu wato anni ita ta sama mata relief a zuciyarta,saidai tana jin ta wani irin sake tsanarsa,ta kuma sake tsanar hada komai dashi. Gabanta ya tako,abinda ya sanya amna gocewa da sauri tunda ita ke first seat da zummar yin gaba "Karki fita......ki jirata" Ya fadi da husky voice dinnan nasa data sake dakewa,tun daga tashinsu daga lagos din bayan wancan abun daya faru zuwa yanzu tana ankare da hamman nata. Sai dacin rai kawai yakeyi wanda shi kansa baisan yana yi ba,jifa jita take satar kallonsa,har a sannan kuma ta tabo sabreen "Adda........wai dama haka hamma yake da kishi?,daga cewa you look familiar?.....haka hamma yake sonki?" Ta fada tana murmushi kaman abun yana burgeta. Sau daya tak ta kalli fuskarsa sanda yake fama da system dinsa,saita maida idanunta ga window din jirgin tana duban yadda suke dai da daidai da gajimare. Abun yana burgeta,tunda shine karon farko data fara keta hazo......saidai can qasan ranta yana cunkushe da halayensa. "Ba kishi bane.....izza ce wulaqanci da kuma izgili.....har yanzu banga wani kyakkyawan halayensa guda daya ba......koma dai meye saura kwanaki kadan suka rage na barshi shi da halinsa dama tarin dukiyar dake sanyashi dagawa izgili da girman kan ma" Tayi dukka maganar a ranta,amma a fili murmushi kawai ta yiwa amna. Amnan bata damu ba taci gaba da dauko mata gulmarsa kadan kadan,tunda ta saba da halinta na wannan fannin. Ba komai sabreen din ke bude baki ta bada amsa ba a maganganu da dama. To a yanzun da yake tsaye a gabanta bata dubeshi,sam bata qaunar hada idanu dashi. "Ko meye zakiyi a yanzu ki dinga tunawa akwai igiyata a kanki......bazan kuma lamunci kowanne abu da zai zama tozarci ga igiyata ba......zan iya daukan kowanne mataki mara dadi muddin kikayi wani abu daya sabawa shari'a......ki kula,ki kula da kyau". Kasa jurewa tayi,haka siddan daga saukarsu a qasar,kowa ya sauka da walwala itama ta samu ta fara tattalin tata zai watsa mata ita. Fararen idanunta ta daga ta watsa masa wani.kallo tsakiyar idanu. Wani haske suka fitar sosai saboda fushin dake cikinsu,wani salon kallo da baiyi kama da harara ba,shi kuma ba kallon banza ba. Ta motsa siraran lips dinta zata ce wani abu,sau kuma taga hakan baida ma wani fa'ida......bata da sauran lokacin batawa,don haka ta soma qoqarin rab'eshi ta fice. Sosai taji an damqi hannunta da wani tsatsauran riqo,ta waiwayo da hanzari tana dubansa,ya damqeta ne ba tare da ya ko waiwayo ya kalleta ba,qeyarsa kawai take iya gani,da hannu daya ya jawota ya dawo da ita gabansa,ya sanyata a tsakanin idanunsa yana mata wani irin kallo da taji ya tsaye mata a sassan jikinta,ya kuma soma sauke rashin kunyar da taji tana taso mata "Duk sanda kika sake gangancin wuceni ina magana.....na rantse da Allah sai na gwada miki ina da banbancin da lusaran mazan barikinki marasa daraja......dole ki amsa min kowacce magana kaman yadda nakeso.....don banajin muryarki tafi tawa tsada ko daraja.....ko banza adadin mazan da sukaji muryarki baikai adadin matan da sukaji tawa ba......kinjini?!" Ya furta da dan tsauri idanunsa na kallon wani gurin daban sabanin cikin idanunta "Eh naji" Ta amsa a sanyaye kanta yana kallon qasa. Shigowar farouq ta gani daga bayansu,wanda ta tabbatar shi bai gani ba,sai ya sakar mata hannun yana juyawa gami da takawa a hankali yana ficewa a jirgin. Hawayen da take riqewa ne suka yiwa kansu da kansu hanya. Ta sanya tissue tana daukesu "Ya isa......ya isa" Take gayawa kanta da kanta. Tana cin alwashi a ranta ko ya bata takardarta.....ko bai bata ba,sauna sauka a nigeria zaman aurensu ya qare......ko ya sallameta ko bai sallameta ba wannan duka damuwarsa ce,alwashi ta ciwa kanta.....wannan karon babu abinda zai dakatar da ita......ba kuma wanda zai hanata. A hankali ta fara takawa itama tana nufar qofa da shimfidadden matakalar da aka jinginewa jirgin. A nutse take sauka tana qoqarin daidaita mode dinta gudun saka damuwa a zukatan amna da anni. Three pieces turkish gown ne a jikinta,wadda take hade da strips skirt da kuma blouse data zauna daidai jikinta,tayi kuma took in da ita kaman yadda tsarin kayan yake,sannan ta kawo doguwar gown din kayan me budadden gaba data sauka har qasa ta kuma bude sosai daga qasan. Qafafunta high hill ne masu madauri da suka dace da kalan rigan. Sosai kayan suka karbeta,baka ganin komai sai fuskarta,zaka rantse da Allah bata hada nasaba ta kusa ko ta nesa da nigeria ba. "Wallahi anni adda sabreen kyau takeyimin......komai nata me kyau ne.....duk kayan data saka sai naga kaman don ita aka yisu" Ta fadi maganan tana matsawa kunnen anni,saidai fuad dake tsaye daura dasu yaji abinda ta fada din. Haka kawai ya samu kansa da daga kan nasa,suka kuma yi masa jagora a kanta duk da yadda yake qoqarin hana hakan faruwa. A kasalance take tafiya saboda bacin rai,sai hakan ya sake zama kaman cikar adon tafiyartata. Idanunta suna lumshewa kadan gami da bude kansu duk a qoqarinta na hana zuciyarta karyewa,ta kuma hana idanunta zubda ruwan hawayen da takeji suna tattara kansu. Amna dake mata murmushi ta maidawa martanin murmushinta,abinda ya sanya pink lips dinta motsawa kadan. "Ya salam" Ya fada can qasan ransa saboda tsigar jikinsa da yaji ta zuba yarrrr.....tun daga tafin qafarsa har zuwa tsakiyar kansa. Wanccan ranar ya tuna.......ranar daya sanya lips dinsa saman nata......shi.kadai yasan me yaji,shi kadai yasan yadda ya iya qwace kansa daga yanayin daya shiga......yayi imani a ranar inda ace shi din manemin mata ne,baisan adadin mata nawa zai nema ba a ranar.....inda shi mashayi ne,baisan adadin kwalba nawa zaisha ba......inda ace shi din asharari ne bayajin cikin kwana uku ma wata macen zata sauke masa abinda yaji a jikinsa a wannan lokacin. Bayajin zai iya ci gaba da tsaiwa a wajen bare ta fahimta ko farouq ya gano canzawarsa,don haka sai ya juya kawai yana takawa a nutse yana matsawa daga wajen gami da sake kame kansa da kyau gudun zubewar kima. Dukkaninsu motar da tazo tararsu ta dauke,mota ce me seat kusan hudu bayan wajen hutawa daga can baya. Shi da farouq suna seat guda,sabreen anni da amna suna set na qarshe. "A ina ka samar mana gida?" Fuad dake gyara agogon hannunsa ya tambayi farouq. Takardun hannunsa ya fara budewa daya bayan daya kafin yace yana tsaida idanunsa akan wata takarda guda daya. "RANGALI ISLAND RESORT......garden villa na masa mana gida.....baiyi tsada cancan ba,duk da Maldivian Rufiyaa mukayi cinikin,ahmad ne ya siya gidan ta hannun wani,da nayi converting kudin da naira sai naga basuyi yawa ba" . Kai kawai ya jinjina,farouq akwai iya aiki,musamman idan akazo batu na tafiya tourism. "Ina fatan yalwatacce ne,kasan mun sake qaruwa this time?". Idanu ya zuba masa,kaman yace masa waye ya qarun da sukayi yawan da zaa nema bangajejen gida?,amma sai yaga kulashi ma bata time da plan ne,don haka ya bishi da " Yes" Kawai farouq yace masa yana boye dariyan dake qasan ransa. Idanunta akan hanya sanda suke wuce lafiyayyun hanyoyin da suka sha banbam dana qasarmu nigeria. Ko daga iya nan ta tsaya ta tabbatar wata duniya ta daban ta shigo. Ta shigo wata duniya da tayi nisa qwarai da tata DUNIYAr data rayu cikinta. Qarfi da yaji takeson komawa 'yar qauye,ta sauke nannauyan ajiyar zuciya sanda motarsu ke shiga wani street me dauke da lafiyayyar hanya da wadatar tsirrai. daga gefe da gefan hanyoyin tana iya hangen ruwa can nesa dasu,wani irin ruwa dake bada blue colour,bata sani ba.....color dinshine haka ko kuma 'yar tazarar dake tsakaninsu take nuna mata haka. Daidai qofan wani madaidaicin kyakkyawan gida motar ta fara slow kafin ta samu wajen tsaiwa. Su suka fara fita suka jira fitowar anni,sannan ita da amna suka biyo bayanta. Tare suka jera da farouq har qofan gidan su kuma suna biye dasu,jordan da drivern motar suna biye dasu da luggage dinsu. Dab da zasu isa qofan gidan qofar ta bude da kanta. Farin matashi ne ya bayyana wanda duka duka shekarunsa ba zasu haura talatin da takwas ba,daga gefansa musaddiq ne da suka jero tare,wanda kamanninsa da fuad ta wasu bangarori da yawa suke bayyana kansu. Yana sanye da jeans da shirt yayin da musaddiq jikinsa ke sanye da jallabiyya saqar marocco,kansa kuma akwai qaramar hular da mukafi mata laqabi da tashi ka fiya naci haka ma mutumin dake gefan musaddiq din. Akwai haske sosai saman fuskar tashi dake bayyana musulunci tattare dashi. Da sassarfa musaddiq din yake qarasowa garesu,idanunshi duka suna kan anni,yana isowa gaban nata baiyi duba da wani girmansa ba,ya bude dukka hannayensa ya rungume annin yana fadin "I missed you so much anni......sai naji kaman ba zakuzo ba.....kwana biyu kawai amma sai naji tayi nisa" Murmushin dake shimfide kan fuskarta kadai ya isa ya gaya maka farincikin dake ranta na ganinsa da tayi,zallar qauna irin wadda ba kasafai ake samunta wajen wani ba idan ka dauke uwa. "Kayi nisan kiwo yaro na......ka tayani roqon hammanku kada ya sake daukemin kai har haka" Ranqwafowa yayi wajen fuskar annin,yana yin qasa qasa da muryarsa don kada fu'ad yaji "Na rantse anni nima bazan sake yarda ba.....ki jawa danki kunne" "Kai kai......hamman?,ai kuwa kaman a kunnensa" Amna data zuro musu kai ta fada tana raba idanu. Duban amna yayi yana dan yamutsa fuska "Bama haka dake auta......kinsan ni dake duk muna together" Ya furta yana daga mata yatsunsa biyu cikin salon son samun goyon bayanta. Fuska ta shagwabe tana cewa "Zan iya haqura nayi shuru idan tsarabata tafi ta kowa yawa" Tayi maganar tana kashe ido daya sannan ta dora "Idan kuma ba haka ba.....ga addana a gefe,ita zan gayawa ta shaida masa abinda kace da mijinta" Ta qarasa maganar tana nuna sabreen da yatsa. Sai a sannan ta lura da sabreen din dake gefansu. Ya dora idonshi a kanta yana dan kafeta da kallo na wasu sakanni. Sosai yaji yasan fuskartata,ba yau ne ranar farko daya fara ganin fuskar ba. Cikin qasa da second biyar ya tuna inda ya santa. Tabbas bazai taba iya mantawa da fuskar ba.....fuskar data dinga fada saboda lafiyar anninsu.......fuskar data zama silar ceto rayuwar anninsu,to amma kuma sai yaji kaman bai kamata farat daya haka a matsayinsa na baquwar fuska a gareta yayi gaggawar tuhumarta inda ya santa ba.....ballanta ma ita din da take matsayin yaaya a wajensa. "Tuba naki adda.....ayimin aikin gafara.....da gaske hamma baida dadi shi yasa takeson hadoni dashi" Ya fada yana hade hannayensa duka biyu waje daya. Batasan ya akayi murmushi ya qwace mata ba,murmushin daya afku saman idanun fu'ad dake dan nesa kadan dasu yana karbar takardu hannun ahmad tare da sake karbar wasu bayanai,don tuni farouq ya wuce cikin gidan yana sake duba yanayinsa. *_DUNIYATA LITTAFIN KUDI NE(PAID BOOK),KAI TSAYE KI TUNTUBI WANNAN NUMBER_* 08187255862 69 Wani abu ya hadiye da baisan meye shi ba,wato ita duk inda taga maza sakin jikinta takeyi?,a ina tasan musaddiq da daga haduwar farko xata sake masa fuska da murmushi har haka?. Idanu ya xuba mata yana kallon yadda take duban musaddiq kai tsaye. "Anyi maka.....amna ma na tabbatar tsokanarka take,don kullum cikin kewarka take,nasha labarinka a wajenta sosai". Ta fada har zuciyarta tana mamakin family din. Kowa na gidan kenan me kirki ne,shi kadai ne maras kirki,maras fara'a,marason jama'a?. Ta tambayi kanta sanda idanunta ya sauka a kanshi. Cikin sa'a idanunsu suka sarqafe guri guda,kusan tare kowa ya dauke dubansa daga kan dan uwansa,sai ya miqa hannu yana karbar takardar hannun ahmad. Da yaren dhivehi asalin harshen mutanen qasar ahmad din yake masa godiyan da batasan ta mece ba. Ga mamakinta sai taji ya maida masa shima da yaren sannan ya ya soma takawa shima yana wucewa ciki da qasaitaccen takun nan nasa. Tana jin muryar musaddiq yana fadin "Godiya nakeyi" Tare da maida kansa ga anni. "Zan kamaki,saikin gayamin dalilin da yasa kina kewata amma baki taba fadimin ko sau daya ba". "Diyata zo mu wuce ciki,wadannan idan kika biye musu zaki wuni a tsaye ne kam" Anni ta furta tana saka hannunta ta kamo hannun sabreen suka fara wucewa cikin gidan. Duk kunyar anni sai ta kamata,tayi qasa da kanta tana biye da ita. Batasan wani abu a duniya da takejin nauyinsa haka ba kaman annin,tana da wani kima a idanunta na musamman. "Yanzu nake shirin leqawa na kiraki ki shigo ciki......wancan shirmammiyar tunda ta hadu da dan uwanta kuma ai shi kenan.....may be daga nan ma yawo zasu wuce iyayen zumudi". " Saddiq....." Fu'ad dake zaune hannun kujera yana duba takardun daya karba yayi kiran Sadiq dake qoqarin daukan ruwa a fridge. Samun kanta tayi da lumshe idonta,batasan me yasa muryarsa take mata nauyi da yawa ba,ba ita ya kira ba,amma sautin kiran yakai mata har tsakiyar qirjinta. Muryarsa tana da wani irin amo me ratsa mutum koda ba dakai yake magana ba. "Na'am" Sadiq yabar abinda yakeyi ya waiwaya yana dubansa,bai daga kai ya kalleshi ba yace "Fita ka gayawa musaddiq kada suje ko ina" "Okay" Ya fada yana ajiye ruwan gami da kama hanyar fita. Numfashi kawai ta aje tana tabe baki,kowa a sake yake amma bandashi,ya iya bada umarni,daga wannan sai wancan,kuma yana iya gama magana dakai kaf ba tare da ya kalli fuskarka ba,ta rasa wanne irin mulki ne haka a cikin jininsa?. Idan kuma muguntarsa ya motsa,ta lura kowa ma da idanu yake hukuntashi,ko don yasan akwai wani abu me nauyi a cikin kallonsa oho?,saita dauke kai gefe tana tabe baki,idanunta kuwa suka sauka kan wani glass door wanda daga nan kana iya hangen wani ruwa nesa kadan dasu dake lullube da farin yashi kaman ta miqa hannu ta kamo. "Gidan ya miki anni?" Ya fada yana sauke takardar daga fuskarsa bayan ya gama jan ajin nasa. "Tubarkallah ma sha Allah" Anni ta fada cikin walwalar data bayyana har saman fuskarta tana kallon kowanne sashe na gidan "Allah ya qara rufa muku asiri duniya da lahira.....Allah ya ninka albarka cikin rayuwarku" "Allahumma ameen" Suka fada shi da farouq a kusan tare. "Anni ta shiga ta huta.....akwai awa kusan daya da rabi kafin sallar magarib.....inajin yau ba wanda zai fita sai gobe idan Allah ya kaimu" Ya fada yana duba agogon hannunsa sannan ya sauke. Cikin aljihun trouser dinsa farouq ya sanya hannu ya ciro key,ya kuma nufi wani daki cikin dakunan dake parlor din,ya bude dakin ya tura qofan yana duban amna "Ja luggage dinki dana anni kikai muku ciki" Yace da ita daidai sanda take shigowa, Amsa masa tayi to tana yin yadda yace din,ya waiwaya yana kallon musaddiq da musaddiq "Bude dakin can musaddiq ku sakawa addanmu nata kayan" Ya fadi yana miqawa musaddiq din key din,sannan ya kalli Sadiq "Saka mana namu a dakin musaddiq sai muyi squatting......addanmu ki shiga ki huta" Ya fada cikin murmushi da girmamawa fal muryarshi,qasan ransa kuma wasai da yadda plan dinsa ya tafi daidai. Harde hannayensa yayi kawai a qirji yana qarewa farouq kallo,wato abinda ya tsara ma ran shi zaiyi kenan?,shi yasa koda ya buqaci picture ko video na gidan ya hana mishi gani. Yasan sarai shi fu'ad din yake kalla,ya kuma shiryama koma meye zaice ko zaiyi,don haka ya basar yaqi kallonsa kaman baisan ma yana a wajen ba. Fridge kawai ya bude yana duba meye da meye a ciki yana kuma masa lissafin me dame ya kamata su ajiye na kwanakinsu a qasar. Wani haushi ya cikashi,ya cika yayi fam da rainin hankalin da farouq din ya shirya masa. To amma a yadda yaga farouq din ya tabbatar ya shiryawa duk wani rigimarsa ne,so dole ya fara bin komai a hankali,tunda basu kadai bane,akwai anni,bazaiso kuma anni taji ko taga komai ba. "Wanne irin gida ne wannan farouq?" Ya fada calmly yana qoqarin danne takaicinsa. Sai daya ajiye gorar hannunsa sannan ya waiwayo yana dubansa "Me fa?" Yayi tambayar kansa tsaye. Sai daya lumshe idonsa ya bude lokaci guda yana jin takaicin rainin wayon farouq da idan ya motsa tsaf xai iya cewa ma bai sanka ba. "3bedroom?,why not a siya me 4bedrooms farouq?" "Akwai baquwar halitta ne a cikinmu da bata samu waje ba?". Kai fu'ad ya girgiza yanason gajarce maganar,don ciki yakeso ya shiga yayi bacci ko na awa daya ne "Babu.....amma dakunan sunyi kadan.....kafi kowa sanin bana iya hada daki da kowa ba ko tun ba yau ba?" "To dawa na hadaka.....kajimin mutum zaimin sharri" Rainin hankalin farouq yakai masa ko ina,yana dab da bashi naushi idan baiyi wasa ba,sai ya ware hannunsa daga qirji yana dubansa "Ka canza plan dinnan,ta koma dakinsu anni tayi squatting tare dasu,saddiq su kwana da musaddiq.....kai kuma muje mu kwana tare". Baya yaja da sauri yana zare ido kaman yaga abun tsoro. "Mu kwana da kai?,alfanun uban me zanyi maka fu'ad?,me zakaji da kwana da namiji gardi dan uwanka bayan ga halalinka a gefe?" Maganar ta fara girmar kunnuwan fu'ad,tun ba yau ba yasan farouq idan baiso ba tantirin kansa ne,baisan sanda hannunsa yakai kan cup din da saddiq yasha ruwa ba ya jefeshi dashi,Allah yasa yana da zafin nama ya cafe "Na rantse da Allah xan ruguza maka kai......kai wanne irin dan iska ne?,maganan da nake maka daban yadda zaka juyan zance daban?,ta yaya zan kwana da wata alhalin muna muhalli daya da anni?". Dariya tana cin farouq amma ya maze "To ba dole nace haka ba?,ga mace me namiji zai maka?,nima bazan kwana da gardi ba,ka cire riga wannan qattin muscles din naka suyita bawa mutum tsoro.....in fact ma ni na fara rehearsal na yadda zan fara kwanciya daga ni sai fannah ta....anni kuma da kake magana akwai wanda zai kaita son ganinku tare....ko turmusheta kayi a gabanta ai saidai tabar muku gurin da gudu.....banson gulma banson k......" Bai qarasa ba yaji saukar abu a qeyarsa,agogon hannunsa ya kwance ya sake jifansa dashi don ya rasa dame zai jefeshi wannan karon. Dafe wajen yayi ya waiwayo yana dubansa fuska a hade "Amma dai kasan wannan zallar cin zali ne ko?,ni nakar xomon?,kaje ka yiwa anni bayanin abinda yasa zaka aikota kwana da ita daki daya mana da kanka". "Ya isheka farouq" Ya fada yana nunashi da yatsa,alamun ya fara qureshi. "Oho" Ya fada yana sungumar ruwansa yayi dakinsu baiko sake waiwayoshi ba. Shuru ne ya ratsa falon bayan wucewar farouq din,sai motsinsu kadan kadan da yake jiyowa daga dakunansu. Maganar gaskiya farouq ya cuceshi,inda kuma yasan da wannan da tuni ya sanya an canza musu gida da yafi haka yawan dakuna kafin su qaraso. Miqewa yayi abisa dole yana soma dosar dakin,abu daya ya sani shi bayason takura,yana son bajewa sosai ya sake a duk inda ya zabi rayuwa,so wanzuwarta cikin dakin kuwa bazai bari ya zama silar hanashi sakewa ba. *Maamah* Sake juya tickets din hannunta tayi guda biyu tana sake qare masa kallo. Mamaki da wani irin dunqulallen baqinciki yana yayyanka zuciyarta. Ta rasa wanne hamshaqinne ya juya tafiyar daga farkonta ta koma qarshe?. Maldevis shine waje na farko da zasu je a qa'ida kaman yadda ta samu tabbacin dukka iyalin gidan alhj hamza kibiya can suka wuce.....saudiyya kuma shine waje na qarshe da zasu ziyarta daga nan kuma sai gida Nigeria,amma wanne hamshaqinne ya karkatar da tata akalar tafiya daga saudiyya kafin ta sauka maldevis sannan su rankaya su wuce turkey tare?. "Hajiya ameena.....tabbas wannan aikin ameena ne" Ta fadi tana jin wutar qiyayyar matar tana sake ninkuwa a ranta. Zazzafar iska ta furzar tana fitar da idanunta waje irin na zallar takaici da kuma tunani. Ita kuwa ta yaya zata dagawa ameena qafa?,ta yaya zata bar ameena taci gaba da shaqar iska cikin aminci?,ba ragi tsakaninta da ameena har abada......yadda bata barta ta samu cikakken iko da mulki da 'ya'yanta ba.....tabbas haka zata zama silar tarwatsa nata ahalin gaba daya,duk wanda ya gaya mata cuta ba shakka ita mutuwa zata gwada masa,sai kawai taja wayarta tana laluben fareeda,tana jin wannan karon a gaban idanun ameenatun zata gwada mata nata izzar da qarfin mulkin kasancewar uwar data dauki cikin fu'ad tayi naqudarsa ta kuma haifeshi.......a gaban idanun kowa zata gwadawa sabreen ta isa da danta......zata nuna mata kuma tana da ikon sanya yaronta ya auri mata d'ai d'ai har guda uku rigis bayan ita. Shuru fareeda tayi tana sauraren bayanan maamah,saidai kuma zuciyarta cike fal da bacin rai da baqin kishin sabreen. Wata zazzafar iska ta furzar tana ajiye bututun shisha dinta ta gyara zamanta "Maldives ai gida ne......ina da sauran visa din qasar da ban gama cinyeta ba,muddin na samu ticket jibi warhaka ina can......ko ba ticket zan sanya daddy yamin hiring private jet......kya sameni a can" Daga haka ta yanke wayar tana latsa wayarta ba bata lokaci tana neman number wayar daddy din nata. Tafasa kawai zuciyarta takeyi,wannan karon da zafi zafinta zata shiga,zata budewa sabreen aiki sosai kaman yadda zata budewa fu'ad,tana jin komai mai sauqi ne......amma zata bari ta tabbatar da samun private jet ko ticket to Maldives. Bugu daya rak ya daga,ba kasafai ta fiya masa sallama ba,kusan sallamarta kiran sunansa ne "Daddyyyy.....maldevis" Ta fada da wata irin shagwaba kamar yarinyar da aka Haifa jiya jiya "Mamana......maldevis a daren nan?" "Daddy gobe......ina da sauran visa na da kamin last two months.......ticket kawai daddy nakeso......please daddy,it's an urgent need daddy". Murmushi ya saki yana juya kai kafin yace "Wani irin emergency issue ne haka ya taso mamana.....nifa mamana yanzun duk hankalina yana kan aure,kiyi aure haka mamana.....ki zabi duk kalar mijin da kk so zan tsaya miki" Maganar sai taji kaman tazo akan gaba,ta saki dariya tana cewa "Nayi maka alqawari daddy.....indai na samu wucewa Maldives gobe ko jibi,ina dawowa zan gabatar maka da mijin da zan aura" "Really mama na?!" Ya tambaya da excitement cikin muryarsa "Yes dad.....na taba maka qarya ne?" Ta sake fada cikin narke murya "No mamana......bani minti goma.....i will get back to you" "Thank youuuuuuu" Ta fada da sautin dariya tana sauke wayar. Lips nata ta cinje tana duban wayar gami da saqa abubuwa iri daban daban akan fu'ad. Zuwa sannan ta gama karance halayensa na girman kai da izza,yana da tsananin taurin kan data tabbatar ita din kanta shaida ce,taso koda bata aureshi ba ya bata hadin kai su mori quruciyarsu tare,amma martanin da yayi mata ya mata ciwon data jima tana riritashi a zuciyarta. "Tabbas saina biyo masa ta bayan gida,idan baiyi wasa ba sunansa ne zai fito a next newspapers da magazine ba na waccan karuwar matar tasa ba......tunda shine garkuwarta.......shi din ya kamata na taba qarfinsa" Ta fada da murmushin mugunta tana murza yatsunta bayan ta tabbatar da hukuncin daya fado ranta shine abinda ya kamata ta zartar. Qarar wayarta ya dawo da hankalinta,ta daga da sauri ganin me kiran. Wani ihun murna ta saki sosai tana jin dadi "I love you daddy......thank you so so much......bansan ma ya zan gode maka ba" Ta fada duk a rude saboda jin dadin samun ticket na tafiya Maldives jibi. Tana Lagos don haka ba ita babu bin jirgi zuwa Lagos din,kawai kanta tsaye jibi zata bi qatar Airways zuwa can "Ki kawomin miji kawai bayan kin dawo" "Baka da matsala dad....." Ta fada tana yanke kiran. Tun a daren ta gama komai,ta gama hada komai ta kuma tanadi komai gudun samun matsala goben kada ta tashi da uzurin da zata tashi ba'a daidai ba har ya jawo ta hada kayanta ba daidai ba. *_hmmmmmm,uhmmmmmmmmm_* *_DUNIYATA LITTAFIN KUDI NE(PAID BOOK),KAI TSAYE KI TUNTUBI WANNAN NUMBER_* 08187255862 𝐃 𝐔 𝐍 𝐈 𝐘 𝐀 𝐓 𝐀 _Zafafabiyar_ ̶B̶O̶O̶K ̶2 ⱧɄ₲Ʉ₥₳ 𝙋𝘼𝙂𝙀 70 70 Sam sam bata fahimci daki daya farouq ya hadesu ba sai da ya murda handle din ya shigo cikin sallama. Daidai lokacin da taketa qoqarin kauda luggage din zuwa kyakkyawan gurin ajiyar kaya dake a dakin bayan ta ware scarfs din kanta ta daure sumarta dashi. Kallon juna sukayi,sai kowa yayi qoqarin dauke idonsa daga kan dan uwansa. Haka kawai ta samu gabanta da faduwa,tunaninta kuma ya koma baya na yadda aka kasafta dakunan "Tashin hankali!.....shine part na na?" Ta fadawa kanta da kanta. Sam sam bata taba hango yiwuwar wanzuwarsu a daki daya ba......ita da mutumin da basa ga maciji sam sam,ta yaya zata iya hada numfashi dashi qarqashin rufin daki guda daya?,lallai inda tasan da yiwuwar faruwar hakan wannan kadai a wajenta ya isa dalilin da zai hanata yin tafiyar ma gaba daya. Sakin abinda takeyi tayi ta kuma ware veil dinta ta lullube kanta dashi dukka tana satar kallonsa. Baiko nuna yasan da tsaiwarta a wajen ba,hasalima yanata daddaga labulayen dakin yana laluba sauran gurare irinsu socket na dakin,switch da sauran gurare saboda tsaro,gudun samun wata boyayyar camera da basusan da ita ba. Baisan ta fice ba sai da yaji alamun jan qofar,ya bi qofar da kallo kafin daga bisani ya dauke dubansa daga wajen yana ci gaba da abinda yakeyi. Wannan dukka ba take taken raini bane ba?,amma ba wanda ya jawo masa illa farouq,kuma tabbas zaija kunnensa,bazai yiwu cikin qasashe biyu da xasu sake zuwa a gaba ya qara hada musu guri ba,duk da kusan duka qasashen ba inda baida gida mallakin kansa uku ko hudu,da kansa zai zabi gidan da yakeso saboda gudun faruwar hakan. Sai daya tabbatar da lafiyar dakin sannan ya soma rage kayan jikinsa,don bazai iya bacci haka ba,ko wankan ma bayajin zaiyishi sai idan ya tashi,duk da farouq nason rage masa jin dadinsa.....don da gaske hutu yazoyi,yazo.ya huta inda ba zaa sashi magana bs ko ciwon kai. Turus tayi sanda ta fito parlor din,wayam ba kowa sai dan motsinsu daga dakunansu. Bin duka qofofin dakunan dake kulle tayi da kallo,saita rasa meye abunyi. Da kunya dai ta jewa dakinsu anni wanda ta tabbatar a yanzun suma hutawa sukeyi,idan ma taje tace mata me?. Ba zata zauna daki daya da d'anta ba wanda mijinta ne a qa'ida duk duniya kuma haka suke kallonsu?,wanda sukasan sahihin zamansu mutanene daidaiku.......hatta da amna bata sanya ran ta gama fahimtar komai da komai. Rasa madafa tayi,dole a qarshe kwanyarta ta gaya mata bata da sauran wani abunyi illa ta koma dakin ta rungumi haquri na yau,zuwa gobe saita nemawa kanta dalili da mafitar da zata sanya a raba dakin. Daidai sanda ya isa bakin qofa da zummar kashe switch na qwan ita kuma ta murza qofar ta shigo. Baikai ga kashewa ba,don haka tsaf ta ganshi. Murdadde kuma qaqqarfan muhammad fu'ad jadda,ma'abocin daga qarfe da dukka surar jikinsa ta koma ta qarfafan maza,saidai surar batayi muni ba,ta dace da zatinsa ta kuma shekarunsa. Babu komai a jikinsa sai gajeran wando iyakar cinyoyinsa,gaba daya faffadan qirjinsa dake lullube da ni'imtaccen tattausan gashi ya tare kusan rabin qofar dashi,abinda ya sanyata saura kadan ta fada qirjin nasa,abinda kuma ya saka tsoro ya kusan sanyata shidewa,ta daburce duka cikin qanqanin lokaci,saita juya da hanzari da zummar ficewa a dakin don ba zata juri ganinsa haka ba. Sosai ya raina sanya hannu qwaya daya ya jawota zuwa gabansa,yanzun hakan ma yayi mata,ya kuma ajeta a gefe,ya saka hannu ya murza key din qofar ya rufe dakin,ya cilla key din saman gado sannan ya juya yana kashe switch din. Dakin yayi duhu,saidai duhun bazai hanaka ganin komai dake dakin ba amma bada fitacciyar suffarsa ba. Takawa yakeyi hankalinsa kwance zuwa gadon kaman ba'a tube yake ba "Sannu a hankali wataran zan baki mamaki tunda na hanaki wannan rainin hankalin da kikemin kaman dodo......sai kace a kaina kika taba ganin namiji a t......" Sai kuma bai qarasa ba yaja tsaki sanda yake dora kansa saman pillow hadi da lumshe idanunsa ya sauke numfashi. Komai ta kasa cewa saboda tsoro daya cakude da takaici. Ta zuba ma fuskarsa idanu duk da bata iya ganinta sosai tana jin bacin rai yana taso mata. Ta tsani koda kalma daya ta hadasu shi yasa take kauce masa,don kowacce magana zai gaya mata bame dadi bace a zuciyarta da kunnuwanta. Don kanta ta samu waje ta nade tana curewa guri daya bayan ta gaji da tsaiwa,don tuni yaja duvet ya rufe jikinsa dukka gaba daya har saman kansa. Tsakiyar baccinsa ya dinga ganinta tana nufoshi cikin swimsuit sanda yake zaune daga gaban swimming pool din yana kallonta. Kanta tsaye ta yiwa kanta mazauni saman cinyarsa,yayin da albarkatun qirjinta yake tokare masa fuska da wani irin salo na tsokana,baisan ya akayi ba ya samu kansa da goga fuskarsa a jikinsu,abinda ya tashi kowacce tsiga ta jikinsa kenan,kowacce kafar jikinsa ta soma fidda zufa,ya kuma jawota ya qanqameta da kyau yana cusa fuskarsa tsakiyarsu kaman me neman taimako. Wani birkitaccen salo takeyi masa,wanda ya taimaka wajen fitarsa a hayyacinsa,ya kuma juyeta saman sun lounger din da yake kai,take al'amura suka fara kankama tsakaninsa da ita. Karar fadawar wani abu ruwan dake gabansu shi ya farkar dashi har a zahiri. Idanunsa ya runtse da qarfi yana jin wani abu yana yawo a sassan jikinsa. Yana jin tamkar a yanzun idanu biyu komai yake faruwa,wani irin zazzafan yanayi da ya jima bai tsinci kanshi a ciki ba saboda yadda yake yawaita yin takatsantsan. "Why?,why?" Ya tambayi kansa da kansa muryarsa can cikin maqogoronsa. Me yasa zata biyo shi har baccinsa?,ba zata qyaleshi ya huta ba kenan?. Ko a baya da yake fuskantar irin mafarke mafarken nan......babu guda daya daya taba ganin ainihin fuskar ko gangar jiki,wannan shine na farko da komanta ya bayyanar masa a zahiri. Fitowarta daga toilet shi ya sanya ya ware rinannun idanunsa a kanta. Duk da bata iya ganinsa sosai amma taga alamun ya farka daga baccin. Dama ya kamata ace ya farka din,tunda agogo ya nuna mata lokacin magariba yayi,amma kuma batasan yadda zata tayar dashi ba,to ya samawa kansa lafiya daya farka din. Dakin ya mata duhu saboda yadda duhu ya soma mamaye garin,saita laluba har ta dace da makunnin ta kunna qwan dakin,take haske ya gauraye ko ina tarwai. Idanunsa ya lumshe yana cusa shi cikin pillow "Oh shit" Ya fada qasa qasa. Qoqarin tashi yake kafin hakan takai ga faruwa sai gashi ta rigashi kunna hasken dakin. Ta yaya zai iya tashi ya miqe ya wuce zuwa bandaki a yanayin da yake ciki?,tambayar dashi kansa baisan amsarta ba. A nata bangaren ta gama gajiya da zaman dakin,burinta kawai ya budeta ta fita,bataga wani alfanun zamansu suna musayar numfashi ba idan ba tsabar muguntar nashi bane ya motsa. Ta duba luggage dinta ma sam bata ga hijab ba,sai mayafai ta hada kusan uku dasu zatayi sallar. Ba ita ta hada kayan ba,zata iya cewa batasan ma meye a ciki ba,anni ce ta musu siyayyar duk da uban lodin kayan da suke da wanda ita kanta batasan adadi ba,amna kuma ta shirya mata tace basai ta buda ba ta saka mata komai,ta kuma biye matan bata duba ba. Bashi da wani sauran abinda ya rage illa dole ya tashi din,don haka ya tattara uban duvet din ya nadeshi a jikinsa ya sauka yana wucewa toilet din a gurguje. Ta danyi mamakin shigarsa toilet fa duvet,amma sai kuma sai ta kauda abun daga ranta ta shimfida abun sallah tana jiran lokaci ya qarasa cika. Ya jima a toilet din yana qoqarin ganin yanayinsa ya daidaita,yasha azaba qwarai har ya dinga tunanin anya yau zai tsallake kuwa?. Kowanne jijiya ta jikinsa aikawa take da saqo,sai bayan kusan minti talatin ya samu yanayinsa ya dawo daidai,amma abinda yakeji a jikinsa bai sauya ba tunda jikin bai samu abinda yakeso ba. Dukka jikinsa ya wani mutu qwarai da wata irin kasala data sakar masa da nauyin jiki,haka yayi wanka ya daura alwala ya fito. Sauqinta daya data samu tana sallah sanda ya fito din,don da alama a yanzun ma gaba gadi ya fito abinsa,ya buda kayansa ya shirya cikin Moroccan jallabiyya black me adon golden din zare,ya saka qaramae gold din hula ya feshe jikinsa da turare sannan ya dauki key ya bude qofan ya fice don zuwa su hada jam'i dasu saddiq kaman yadda suka saba duk sanda sukayi tafiya a qasashen daba masallaci a kusa da masaukinsu. Fitarsa sai taji kaman ta samu 'yanci ne,ta kammala sallarta ta fada wanka. Koda ta fito lokacin isha'i yayi,tasan qwarai tana da nauyin wanka,amma na yau ya haura na kullum saboda ba qaramar wahala tasha wajen gane yadda zatayi amfani da kayan bandakin ba. Da karsashinta ta isa ga luggage dinta,saidai kaf ta cajeshi babu wata suturar arziqi da zata iya sakata ta fita,sai uban lingerie data zuba mata kaman karuwar dake neman customer. Takaici ya sanyata komawa ta zauna ta rafka tagumi,kusan mintina ashirin ta kashe a haka kafin ta jawo akwatin ta sake birkiceshi ko zata dace. Baqinciki ya sanyata daga lingerie din daya bayan daya tana qare musu kallo. Kaya ne na rashin kunyar da ita kanta kunyar wasu a ciki takeji idan ta daga "Amna kin kwafsamin.....kin kasheni......shi yasa kikace kada na duba kayan" Ta fada a fili daidai sanda ta daga wata lingerie din da aka yiwa wani yanka na wulaqanci,aka fidda gidan mama daga qasa kuma aka mata wata huda. Shigowarsa da sallamarsa duka lokacin guda ne,ta saki rigar da sauri ya bita da kallo,ta miqa hannu da gaggawa ta tattareta ita da sauran tana zubawa a akwatin sannan ta miqe. Tanason masa maganan ya turo mata amna amma batason halinsan nan,ya kammala abinda yakeyi ya doshi hanyar fita "Idan kin gama abinda kikeyi din ki fito za'ayi dinner" "Don Allah ka turomin amna" Ta katsi numfashi tana fadi da sauri har sai daya waiwayo ya kalleta,karon farko da magana ta nutsuwa da respect harma da begging a ciki ya taba hadasu,sai baice komai ba ya fice abinsa. Harara ta ballawa qofan tana jin baiken kanta,me yasa ma ta roqeshi?,gashinan ya yarfata a banza,dama me hali ai baya fasa halinsa,ta tsugunna tana hade kayan cikin takaici. Saidai ko gamawa batayi ba amna tayi sallama,ta tsaya daga qofa tana leqowa a darare. "Ki shigo malama" Ta furta tana jifanta da harara. "Shigowa makwancin hamma din kai tsaye haka hadari ne" Ta fada tana shigowa kaman yadda ta buqata. Tana mamakin irin tsoronsa da sukeyi da yadda suke kiyayarsa qwarai. "Yau fada zamuyi dake har anni saita shigo sasanci" "Me nayi adda?" Ta tambaya tana waro idanunta gami da dafe qirjinta "Kayan da kika zubamin dama kenan amna?" Ta tambayeta tana dan kama kunnenta. Dafe kunnen tayi dariya tana kamata,duk da riqon babu zafi amma tace "Wayyo kunnen autar anni......aradu anni ce tace duka na zuba miki su,ni kuma da naji tace haka saina kwashe wadancan......bansan mix ya kamata ayi ba" . Kunya ta saukarwa sabreen,sai kawai ta saki kunnen amna din "Saikije ki daukomin hijab dinki,kayan fice ficen ma duk na fasa sakasu tunda baki sakamin kayan zaman gida na arziqi ba,da hijab zanta zama" "Kaina bisa wuya na" Ta furta tana dariya gami da ficewa. Gudun jira sai kawai ta shirya kanta cikin riga da wandon,rigar ta sauko mata har saman mazaunanta,wandon kuma cif jikinta,don ya fidda sigar santala santalan cinyoyinta da faffadan qugunta. Murda qofan ya sanyata juyowa da sauri tana zaton amna ce ta dawo,saidai a maimakon amna din sai taga hammanta. Fuad ne tsaye fuskarsa babu walwala,kai tsaye ya soma kallonta tun daga qasan qafafunta,idanunsa kuma suka cake akan qirjinta,abinda ya sanya yaji wani yarrr tsigar jikinsa ta zuba. Fes abinda yaji da dumi da qamshin da wajen kiyi ya dawo masa fes a qwalqwalrsa,sosai jini ya harba ko ina a jikinsa,yayi gaggawar damqe numfashinsa gami da hana faruwar abinda yake shirin faruwar dashi. Kallon qurillar da a yau yayi mata karon farko a tarayyarsu ya ratsa kowanne jini dake gudu a sassan jikinta. Idan tace zata juya masa baya nan ma tasan bata tsira ba,komai na jikinta ita kañta tayi imanin a bayyane yake. "Karki fara gangancin fitowa a haka......ki nema kinomo ko hijab ki saka a jikinki". Sai ya saki qofar yana juyawa yana jin numfashinsa kaman zai tsaya da aiki. *_DUNIYATA LITTAFIN KUDI NE(PAID BOOK),KAI TSAYE KI TUNTUBI WANNAN NUMBER_* 08187255862 𝐃 𝐔 𝐍 𝐈 𝐘 𝐀 𝐓 𝐀 _Zafafabiyar_ ̶B̶O̶O̶K ̶2 ⱧɄ₲Ʉ₥₳ 𝙋𝘼𝙂𝙀 71 71 Tun kafin ya qaraso idanun farouq yana kanshi,fata ne fal zuciyarsa na daidaituwar al'amura,yasan sarai halin fu'ad......yana da kafiya da taurin kai akan abubuwan da bai fuskancesu ba,amma da zarar ya fuskanta din yafi kowa bawa abun muhimmanci. Ba jiya ko yau suke tare da fu'ad ba,tsohuwar alaqa ce da aka kafata tun basu mallaki hankalin kawunansu ba,mutuwar jiki a wajen fu'ad na fassara abu guda ne tattare dashi,rashin lafiya ta jiki irin ta kowa,da kuma motsawar feeling irin na kowanne lafiyayyen namiji. "Baka da lafiya ne dude?" Farouq ya fada qasa qasa sanda fu'ad ke zama a dining din kusa da farouq din. Qoqarin murjewa yayi yana cewa "Am fine......bacci nayi bai kuma isheni yadda ya kamata ba" "I see..." Kawai ya furta da salon dashi kansa yasan farouq din bai aminta ba. Tare suka jero da amna din suna fitowa,sai ya zare idonsa daga kan wayarsa yana duban sashenta. Baiyi tsammanin zata saka hijab din kamar yadda ya umarta ba,saboda yasam taurin kanta da kafiyarta,sai yaji wani sanyi na ratsashi ganin karon farko tayi abinda yace da ita. Gaida anni ta sakeyi tana rusunawa,sannan suma suka gaidata harda farouq da yake da sauqin kai. Amna ce ta soma servings nasu daga girkin cook din da sukayo hiring anan qasar wato hidaya. Musulma ce data qware wajen sarrafa abinciccikan qasashe da dama. Yawa yawan wadanda takewa aiki masu hannu da shuni ne don ta qware matuqa wajen iya sarrafa tukunya. Da kudi sosai ake daukanta tayi maka iya adadin watanni ko kwanakin da kakeso,amma a wajen mutane irinsu fu'ad din wannan din ba wani aiki bane babba. "Sabreen" Anni ta fada tana dubanta "Na'am anni" "Tashi ki serving mijinki" Wani nauyi taji ta aza mata,amma hakanan ta miqe ta dauki plate ta soma xuba mishin. Tana xubawa tana kallonsa wai ko zaice ya isa haka,amma abun takaici dukka hankalinsa yana kan wayarsa "Qila ma chart yakeyi da fareeda" Wata zuciyar ta raya mata. Wato fareedan ce mutum.....ita tana tsaye saboda shi amma.baida lokacinta?. Duka anni na ankare da komai,abinda ya sake tabbatar mata da tunaninta "It's family time muhammadu....a aje wayar nan haka ko?". Kansa ya daga ya dubi anni yana gyada kai yana sakin qaramin murmushi. Karon farko data gayawa kanta da gaske yana da kyau kaman yadda takeji daga bakin mutane. Bata taba ganin wani abu me kama da murmushi akan fuskarsa ba sai a yau,zancan amna ya sake tabbata na ba wanda yake samun fu'ad din a asalin fu'ad dinsa sai anni. "Is okay" Yace sanda yake maida hankalinsa kan abincin data zuba masan. Abinci sukeci cikin qauna da fahimtar juna,saidai ita din ta koma tamkar bare a cikinsu,hasalima ta kasa sakewa sam,sai juya spoon takeyi. Sai kunnuwa data sanya sanda suke lissafin ina da ina zaa fara fita a goben. Amna keta lissafin abinda zasu kashe "Adda nawa zaa saka miki a account" Amna ta tambayi sabreen,murmushi kadan tayi ta girgiza kai "Ko sisi amna.....me zan siya?" "Tsaraba mana adda.... Akwai traditional market nasu fa,zakiga abubuwa da yawa da zasu burgeki.....kinji anni wai batason komai......adda komai sai tace bataso?". "Musaddiq ka saka mata wani abu itama... Mijinta ya qara mata,idan kuma bata da dolla account saina ara mata nawa guda daya". Anni ta fada tana murmushi,kunyarta tana dada burgeta sosai. Tsam ya miqe abinsa yana dauke wayoyinsa. "Zan kwanta anni" "Mu tashi lafiya,muma kusan kwanciya kowa zaiyi ai dare ya fara" A nan ya barsu ya gangara ya wuce dakinsa,don bayajin sakewa har yanzu a jikinsa. 71 Tun kafin ya qaraso idanun farouq yana kanshi,fata ne fal zuciyarsa na daidaituwar al'amura,yasan sarai halin fu'ad......yana da kafiya da taurin kai akan abubuwan da bai fuskancesu ba,amma da zarar ya fuskanta din yafi kowa bawa abun muhimmanci. Ba jiya ko yau suke tare da fu'ad ba,tsohuwar alaqa ce da aka kafata tun basu mallaki hankalin kawunansu ba,mutuwar jiki a wajen fu'ad na fassara abu guda ne tattare dashi,rashin lafiya ta jiki irin ta kowa,da kuma motsawar feeling irin na kowanne lafiyayyen namiji. "Baka da lafiya ne dude?" Farouq ya fada qasa qasa sanda fu'ad ke zama a dining din kusa da farouq din. Qoqarin murjewa yayi yana cewa "Am fine......bacci nayi bai kuma isheni yadda ya kamata ba" "I see..." Kawai ya furta da salon dashi kansa yasan farouq din bai aminta ba. Tare suka jero da amna din suna fitowa,sai ya zare idonsa daga kan wayarsa yana duban sashenta. Baiyi tsammanin zata saka hijab din kamar yadda ya umarta ba,saboda yasam taurin kanta da kafiyarta,sai yaji wani sanyi na ratsashi ganin karon farko tayi abinda yace da ita. Gaida anni ta sakeyi tana rusunawa,sannan suma suka gaidata harda farouq da yake da sauqin kai. Amna ce ta soma servings nasu daga girkin cook din da sukayo hiring anan qasar wato hidaya. Musulma ce data qware wajen sarrafa abinciccikan qasashe da dama. Yawa yawan wadanda takewa aiki masu hannu da shuni ne don ta qware matuqa wajen iya sarrafa tukunya. Da kudi sosai ake daukanta tayi maka iya adadin watanni ko kwanakin da kakeso,amma a wajen mutane irinsu fu'ad din wannan din ba wani aiki bane babba. "Sabreen" Anni ta fada tana dubanta "Na'am anni" "Tashi ki serving mijinki" Wani nauyi taji ta aza mata,amma hakanan ta miqe ta dauki plate ta soma xuba mishin. Tana xubawa tana kallonsa wai ko zaice ya isa haka,amma abun takaici dukka hankalinsa yana kan wayarsa "Qila ma chart yakeyi da fareeda" Wata zuciyar ta raya mata. Wato fareedan ce mutum.....ita tana tsaye saboda shi amma.baida lokacinta?. Duka anni na ankare da komai,abinda ya sake tabbatar mata da tunaninta "It's family time muhammadu....a aje wayar nan haka ko?". Kansa ya daga ya dubi anni yana gyada kai yana sakin qaramin murmushi. Karon farko data gayawa kanta da gaske yana da kyau kaman yadda takeji daga bakin mutane. Bata taba ganin wani abu me kama da murmushi akan fuskarsa ba sai a yau,zancan amna ya sake tabbata na ba wanda yake samun fu'ad din a asalin fu'ad dinsa sai anni. "Is okay" Yace sanda yake maida hankalinsa kan abincin data zuba masan. Abinci sukeci cikin qauna da fahimtar juna,saidai ita din ta koma tamkar bare a cikinsu,hasalima ta kasa sakewa sam,sai juya spoon takeyi. Sai kunnuwa data sanya sanda suke lissafin ina da ina zaa fara fita a goben. Amna keta lissafin abinda zasu kashe "Adda nawa zaa saka miki a account" Amna ta tambayi sabreen,murmushi kadan tayi ta girgiza kai "Ko sisi amna.....me zan siya?" "Tsaraba mana adda.... Akwai traditional market nasu fa,zakiga abubuwa da yawa da zasu burgeki.....kinji anni wai batason komai......adda komai sai tace bataso?". "Musaddiq ka saka mata wani abu itama... Mijinta ya qara mata,idan kuma bata da dolla account saina ara mata nawa guda daya". Anni ta fada tana murmushi,kunyarta tana dada burgeta sosai. Tsam ya miqe abinsa yana dauke wayoyinsa. "Zan kwanta anni" "Mu tashi lafiya,muma kusan kwanciya kowa zaiyi ai dare ya fara" A nan ya barsu ya gangara ya wuce dakinsa,don bayajin sakewa har yanzu a jikinsa. Wani mummunan horo kawai yakeji farouq yayi masa na hadashi kwana daki daya da ita. Gaba dayansa sai yake jinsa kaman a birkice yake,tun yana qaryata wanzuwarta daki daya dashi ne ya sanya yanayinsa komawa hakan,har yayi amanna cewa hakanne. A dare daya tak ya kasa samin isashen bacci har zuwa wayewar gari,wayewar garin da ya tashi da ninkin rashin kuzari da karsashi a tattare dashi,fiye ma da yadda ya kwana jiya. Kowanne motsi farouq yana ankare dashi,dariya qasan ranshi kaman zata kasheshi. "Duk dacin ranka.....duk miskilancinka halittar mace tafi qarfinka ko kai waye......qaton tuzuru dakai sai taurin kai da kafiyan da ba inda zasu kaika?,dama can sarari ka samu,nisan tazarar dake tsakaninku ya sanya kake ganin kamar baka da wata buqata ko sha'awa irin ta d'a namiji.....wallahi qarya kake fu'ad......a wannan fannin ni kaina na sallama maka.....zan gani idan tusa zata hura huta......daga yau zuwa gobe kawai na baka,if kaci gaba da taurin kai.....nasan matakin da zan dauka a kanka" Farouq yayi dukka wannan gulmar cikin zuciyarsa yana duban fu'ad dake zaune yana kurbar maca and ginseng tea. Kaman baiso yake daga cup din zuwa bakinsa,shi kansa,ranshi a jagule,baiso irin wannan yanayin ya tasammasa a irin wannan lokacin ba sam,saidai koma meye zaya faru bayajin zai yarda koda da wasa ya hada jikinsa da ita. Jikin da akullum ya kalla sai yayita lissafin adadin maza nawa ne suka rabeshi?,adadin maza nawa ne suka tabashi?,dame dame sukayi da ita?. Yana da bala'in qyanqyami na fitar hankali,wannan qyanqyamin ya sanya bayajin shikam ko mata biyu zai iya aura,gwara ya tattara mutuntakarsa a muhalli daya. Uwa uba wani irin kishi ne dashi,ba kuma wai yanzu ba,tun tale tale zai iya cewa da kishin ya tashi,dashi aka halicceshi. Baisan maruka nawa yasha daga hannun maamah ba sanda take kawo maza gidan abokan kasuwancinta da suke siyan shaddodin da ta soma business dinsu ba,baisan adadin yawan dukan da yasha a kansu ba......saboda muddin zaka sanya qafarka a gidansu,to shi kuwa zai kafe ya cake a qofa ya hanaka qarasawa ciki. "Babanmu baya so......ya hana maza shigar masa gida,ka koma ka aiko qanwarka ko yayarka" Wadannan sune lafuzzansa a yayin da fuskarsa kan cika da wani irin fushi da zafin zuciya. Kusan baki suke sakewa,kusan duka duka shekarunsa a sannan ba zasu wuce goma sha daya ba,amma zuciyar manya gareshi,zuciyar data kubuta daga dukkanin tsoro saboda kare martaba da haqqin mahaifinsa. Wani lokacin idan ta jawoshi ta daka ta daka,abbansa dake daki kwance yana jiyya shi zaita kiransa,shi zai lallasheshi,yakan ce "Komai na duniya me wucewa ne me babban suna.....komai kuma haquri ne yake zama silar cin nasararsa......ka daina bari ana tabamin lafiyarka me tsadar nan kaji?" Sau tari duk kalan dukan da zata masan ba kasafai ya fiya kuka ba,duk da cewa duka ne ba kadan ba,wani lokaci harda abinda bai kamata ayi dukan ba. Idanunsa saidai suyi jajir,yayita hadiyar yawu da wani irin tsauri "Abba......gidanka ne fa,ta yaya kana kwance zasu dinga tsallakowa suna shigo maka?" Murmushi yakan yi,duk da yakan tsinci ciwo cikin murmushin nasa "Watarana sai labari me babban suna". Ire iren wadannan hirarrakin da abbansa har yau ya kasa sabawa da tunasu,har yau ya kasa jin Normal ne a rayuwarsa,har yau kansa baya iya jure tunasu,duk sanda sukazo masa sai yaji kaman kansa zai tarwatse,sai ya sakejin wani abu yana sanya nisa me tarin yawa tsakaninsa da maamah din,yakan ji kaman bazai iya qara idanu ya kalleta ko ya mutuntata ba......amma ta wani fannin.........uwa data cancanci a kirata mahaifiya irin ameenatu anni......itace ke riqo da hannunsu a ko yaushe,ta kuma qarfafesu da yi mata biyayya. Rana daya daya fahimci ta fara sana'ar dalilin aure,adadin maza da matan dake kai kawo a gidan suka dadu,a ranar ya yiwa wani mummunan rotsen da da qyara aka kashe maganar a police station. Ranar nisan kwana ne kadai ya kawoshi yau da ake magana,don ta sakashi a daki ne ta masa wani irin duka da sai da ya daina numfashi,tun abban nasu dake daga kwance ba daman tashi ya ceceshi yana kiran sunanta gami da qoqarin dakatar da ita,har yawun bakinsa ya dauke tsaf,yayi shuru ya zubawa sarautar Allah ido,yana jin sautin dukan da maganganunta,amma baya iya jin koda tarin muhammad. Yasan halinsa.....sha wuya ne dake iya shanye zafi da tsananin duka,yasan kowanne irin nau'in azaba take masa bazaiyi magana ba. "Me shegen baqin hali irin na ubansa.......baka isa ka hanani neman kudi ba wallahi,yadda talauci ke neman kai ubanka ramin qabarinsa tun lokacinsa baiyi ba......ni bazan zauna talaucin yayi ajalina ba". Qarshe dai musaddiq ya aika ya dinga zuba masa ruwa kafin ya farfado. Ta dauka zai rusuna daga ranar,amma sai taga kaman ma bashi ta daka ba,sai ya canza sabon salon kora da hali wajen yayyanka musu takalmi,karta mota da sace tayoyin motar ko na babur.......still marasa haquri a cikinsu police station suka.kaishi da qyar ta karboshi,zuciyarsa kuma na a tsaye bai rusuna ba,dolen dole ta tattara ta canza sana'a,waccan din saidai tayi a wani wajen daban amma ba cikin gidansu ba. Ajiye roban maca root din dana ginseng farouq yayi yana kallonsa. "Amma yallabai......wadannan abubuwan biyu kaman suna enhancing libido fa.....and..... ". Wani kallo fu'ad ya watsa masa da idanunshi da sukayi laushi qwarai,ya miqa hannu yana fusge container din ya ajiye a gabansa "Baka lura kuma yana boosting energy ba?" Ya fada cikin jin haushi. Dariya sosai ya qunshe farouq din yana gyada kai kaman qadangare "Yes.....yes na gani,kaman kai kenan da kayi loosing energy dinka ko?.....wannan bazai boosta maka komai ba dude.......you need a......." "Zip it" Ya katseshi da kakkausan kallon nan nasa. Shikam farouq bai gama maganansa ba,baiga abinda zai sanya a hanashi fadin abinda yai niyya ba,sai ya janye baya yana daga kafadu. "Duk wani abu da zai maidaka namijin gaske you're Comsumpting......but ka kasa kunna engine din kadan......" Bai qarasa ba ya cire spoon din cikin mug din ya jefeshi dashi,abinda ya sanyashi kasa qarasa maganan......amma kuma ya kece da dariya,wanda shigowar anni parlor din ya dakatar dashi daga dariyar. "Farouqu.....zoka miqawa muhammadu ya dubamin wannan address din.........wata qawata ce muna magana dazu ashe sun shigo suma". Karbar address din yayi ya kalla,bai gane gurin ba don haka ya miqawa fu'ad. "Few kilometers ne tsakaninmu,zaki je ne anni?" Ya tambaya yana dubanta. "Eh amma sai wajen gobe nake tunani.....tunda yau kaman naji amna tana fadan inda zasuje,ba zaa bar gidan ba kowa ba duk da ba wani abu bane". Kai ya jinjina ya ajiye takardar,sannan ya daga mug dinsa yana shanye ginseng tea dinsa abinsa,ba tare da ya maida kai ga kallon da farouq yaketa binsa dashi ba. Dukkaninsu farouq ya xuba a mota suka fice. Sosai suka zaga garin,guraren da sukaje sun kusa biyar,amma duk da haka amna bata gaji ba,fadi takeyi "Ya farouq.....don Allah mu zaga Maldives gaba daya kafin mu tafi,tunda island ne baida girma can can". Dariya musaddiq ya bushe dashi yana kallonta "Kinsan yawan guraren da suke dashi kuwa amnee......a qalla fa gurare dari da tamanin amnee,yaushe zamu iya zagayeshi?" "But......amma please BB,gobe ma ka fita damu,inason naci rihaakuru fish paste.......kifin Maldives please ya musaddiq" Ta fada tana narke murya. "Ki bani cin hanci mana saina roqar mana shi,harda traditional market dinsu.......rannan naga suna saida abubuwan gargajiya sosai.......i assured zakiji dadin gurin" Maganan musaddiq ta sake gigita amnee,ta dinga roqar farouq,har sai data saka sabreen a ciki. "Please BB farouq......a taimaki autan anni mana" Sabreen din ta fada da sassanyar muryarta dake da wani irin nutsuwa. Murmushi farouq ya saki,tana da kima a idanunsa da martaba me yawa,yana ganin mutuncinta sosai saboda yanayin nutsuwarta da kamun kanta. "An gama tunda.matar.oga ta saka baki" Dariya ya basu dukkaninsu har ita sabreen din sai data murmusa kadan. Har yau ya kasa yarda ko sau daya da binciken fu'ad a kanta......baisan meye dalili ba,duk da ya sani shi din mutum ne mara gaggawa akan kowa da komai......amma gaba daya halayensa sun canza a kanta,bazaice kuma ga wani dalili babba guda daya ba. *_DUNIYATA LITTAFIN KUDI NE(PAID BOOK),KAI TSAYE KI TUNTUBI WANNAN NUMBER_* 08187255862 𝐃 𝐔 𝐍 𝐈 𝐘 𝐀 𝐓 𝐀 _Zafafabiyar_ ̶B̶O̶O̶K ̶2 ⱧɄ₲Ʉ₥₳ 𝙋𝘼𝙂𝙀 71 71 Tun kafin ya qaraso idanun farouq yana kanshi,fata ne fal zuciyarsa na daidaituwar al'amura,yasan sarai halin fu'ad......yana da kafiya da taurin kai akan abubuwan da bai fuskancesu ba,amma da zarar ya fuskanta din yafi kowa bawa abun muhimmanci. Ba jiya ko yau suke tare da fu'ad ba,tsohuwar alaqa ce da aka kafata tun basu mallaki hankalin kawunansu ba,mutuwar jiki a wajen fu'ad na fassara abu guda ne tattare dashi,rashin lafiya ta jiki irin ta kowa,da kuma motsawar feeling irin na kowanne lafiyayyen namiji. "Baka da lafiya ne dude?" Farouq ya fada qasa qasa sanda fu'ad ke zama a dining din kusa da farouq din. Qoqarin murjewa yayi yana cewa "Am fine......bacci nayi bai kuma isheni yadda ya kamata ba" "I see..." Kawai ya furta da salon dashi kansa yasan farouq din bai aminta ba. Tare suka jero da amna din suna fitowa,sai ya zare idonsa daga kan wayarsa yana duban sashenta. Baiyi tsammanin zata saka hijab din kamar yadda ya umarta ba,saboda yasam taurin kanta da kafiyarta,sai yaji wani sanyi na ratsashi ganin karon farko tayi abinda yace da ita. Gaida anni ta sakeyi tana rusunawa,sannan suma suka gaidata harda farouq da yake da sauqin kai. Amna ce ta soma servings nasu daga girkin cook din da sukayo hiring anan qasar wato hidaya. Musulma ce data qware wajen sarrafa abinciccikan qasashe da dama. Yawa yawan wadanda takewa aiki masu hannu da shuni ne don ta qware matuqa wajen iya sarrafa tukunya. Da kudi sosai ake daukanta tayi maka iya adadin watanni ko kwanakin da kakeso,amma a wajen mutane irinsu fu'ad din wannan din ba wani aiki bane babba. "Sabreen" Anni ta fada tana dubanta "Na'am anni" "Tashi ki serving mijinki" Wani nauyi taji ta aza mata,amma hakanan ta miqe ta dauki plate ta soma xuba mishin. Tana xubawa tana kallonsa wai ko zaice ya isa haka,amma abun takaici dukka hankalinsa yana kan wayarsa "Qila ma chart yakeyi da fareeda" Wata zuciyar ta raya mata. Wato fareedan ce mutum.....ita tana tsaye saboda shi amma.baida lokacinta?. Duka anni na ankare da komai,abinda ya sake tabbatar mata da tunaninta "It's family time muhammadu....a aje wayar nan haka ko?". Kansa ya daga ya dubi anni yana gyada kai yana sakin qaramin murmushi. Karon farko data gayawa kanta da gaske yana da kyau kaman yadda takeji daga bakin mutane. Bata taba ganin wani abu me kama da murmushi akan fuskarsa ba sai a yau,zancan amna ya sake tabbata na ba wanda yake samun fu'ad din a asalin fu'ad dinsa sai anni. "Is okay" Yace sanda yake maida hankalinsa kan abincin data zuba masan. Abinci sukeci cikin qauna da fahimtar juna,saidai ita din ta koma tamkar bare a cikinsu,hasalima ta kasa sakewa sam,sai juya spoon takeyi. Sai kunnuwa data sanya sanda suke lissafin ina da ina zaa fara fita a goben. Amna keta lissafin abinda zasu kashe "Adda nawa zaa saka miki a account" Amna ta tambayi sabreen,murmushi kadan tayi ta girgiza kai "Ko sisi amna.....me zan siya?" "Tsaraba mana adda.... Akwai traditional market nasu fa,zakiga abubuwa da yawa da zasu burgeki.....kinji anni wai batason komai......adda komai sai tace bataso?". "Musaddiq ka saka mata wani abu itama... Mijinta ya qara mata,idan kuma bata da dolla account saina ara mata nawa guda daya". Anni ta fada tana murmushi,kunyarta tana dada burgeta sosai. Tsam ya miqe abinsa yana dauke wayoyinsa. "Zan kwanta anni" "Mu tashi lafiya,muma kusan kwanciya kowa zaiyi ai dare ya fara" A nan ya barsu ya gangara ya wuce dakinsa,don bayajin sakewa har yanzu a jikinsa. 71 Tun kafin ya qaraso idanun farouq yana kanshi,fata ne fal zuciyarsa na daidaituwar al'amura,yasan sarai halin fu'ad......yana da kafiya da taurin kai akan abubuwan da bai fuskancesu ba,amma da zarar ya fuskanta din yafi kowa bawa abun muhimmanci. Ba jiya ko yau suke tare da fu'ad ba,tsohuwar alaqa ce da aka kafata tun basu mallaki hankalin kawunansu ba,mutuwar jiki a wajen fu'ad na fassara abu guda ne tattare dashi,rashin lafiya ta jiki irin ta kowa,da kuma motsawar feeling irin na kowanne lafiyayyen namiji. "Baka da lafiya ne dude?" Farouq ya fada qasa qasa sanda fu'ad ke zama a dining din kusa da farouq din. Qoqarin murjewa yayi yana cewa "Am fine......bacci nayi bai kuma isheni yadda ya kamata ba" "I see..." Kawai ya furta da salon dashi kansa yasan farouq din bai aminta ba. Tare suka jero da amna din suna fitowa,sai ya zare idonsa daga kan wayarsa yana duban sashenta. Baiyi tsammanin zata saka hijab din kamar yadda ya umarta ba,saboda yasam taurin kanta da kafiyarta,sai yaji wani sanyi na ratsashi ganin karon farko tayi abinda yace da ita. Gaida anni ta sakeyi tana rusunawa,sannan suma suka gaidata harda farouq da yake da sauqin kai. Amna ce ta soma servings nasu daga girkin cook din da sukayo hiring anan qasar wato hidaya. Musulma ce data qware wajen sarrafa abinciccikan qasashe da dama. Yawa yawan wadanda takewa aiki masu hannu da shuni ne don ta qware matuqa wajen iya sarrafa tukunya. Da kudi sosai ake daukanta tayi maka iya adadin watanni ko kwanakin da kakeso,amma a wajen mutane irinsu fu'ad din wannan din ba wani aiki bane babba. "Sabreen" Anni ta fada tana dubanta "Na'am anni" "Tashi ki serving mijinki" Wani nauyi taji ta aza mata,amma hakanan ta miqe ta dauki plate ta soma xuba mishin. Tana xubawa tana kallonsa wai ko zaice ya isa haka,amma abun takaici dukka hankalinsa yana kan wayarsa "Qila ma chart yakeyi da fareeda" Wata zuciyar ta raya mata. Wato fareedan ce mutum.....ita tana tsaye saboda shi amma.baida lokacinta?. Duka anni na ankare da komai,abinda ya sake tabbatar mata da tunaninta "It's family time muhammadu....a aje wayar nan haka ko?". Kansa ya daga ya dubi anni yana gyada kai yana sakin qaramin murmushi. Karon farko data gayawa kanta da gaske yana da kyau kaman yadda takeji daga bakin mutane. Bata taba ganin wani abu me kama da murmushi akan fuskarsa ba sai a yau,zancan amna ya sake tabbata na ba wanda yake samun fu'ad din a asalin fu'ad dinsa sai anni. "Is okay" Yace sanda yake maida hankalinsa kan abincin data zuba masan. Abinci sukeci cikin qauna da fahimtar juna,saidai ita din ta koma tamkar bare a cikinsu,hasalima ta kasa sakewa sam,sai juya spoon takeyi. Sai kunnuwa data sanya sanda suke lissafin ina da ina zaa fara fita a goben. Amna keta lissafin abinda zasu kashe "Adda nawa zaa saka miki a account" Amna ta tambayi sabreen,murmushi kadan tayi ta girgiza kai "Ko sisi amna.....me zan siya?" "Tsaraba mana adda.... Akwai traditional market nasu fa,zakiga abubuwa da yawa da zasu burgeki.....kinji anni wai batason komai......adda komai sai tace bataso?". "Musaddiq ka saka mata wani abu itama... Mijinta ya qara mata,idan kuma bata da dolla account saina ara mata nawa guda daya". Anni ta fada tana murmushi,kunyarta tana dada burgeta sosai. Tsam ya miqe abinsa yana dauke wayoyinsa. "Zan kwanta anni" "Mu tashi lafiya,muma kusan kwanciya kowa zaiyi ai dare ya fara" A nan ya barsu ya gangara ya wuce dakinsa,don bayajin sakewa har yanzu a jikinsa. Wani mummunan horo kawai yakeji farouq yayi masa na hadashi kwana daki daya da ita. Gaba dayansa sai yake jinsa kaman a birkice yake,tun yana qaryata wanzuwarta daki daya dashi ne ya sanya yanayinsa komawa hakan,har yayi amanna cewa hakanne. A dare daya tak ya kasa samin isashen bacci har zuwa wayewar gari,wayewar garin da ya tashi da ninkin rashin kuzari da karsashi a tattare dashi,fiye ma da yadda ya kwana jiya. Kowanne motsi farouq yana ankare dashi,dariya qasan ranshi kaman zata kasheshi. "Duk dacin ranka.....duk miskilancinka halittar mace tafi qarfinka ko kai waye......qaton tuzuru dakai sai taurin kai da kafiyan da ba inda zasu kaika?,dama can sarari ka samu,nisan tazarar dake tsakaninku ya sanya kake ganin kamar baka da wata buqata ko sha'awa irin ta d'a namiji.....wallahi qarya kake fu'ad......a wannan fannin ni kaina na sallama maka.....zan gani idan tusa zata hura huta......daga yau zuwa gobe kawai na baka,if kaci gaba da taurin kai.....nasan matakin da zan dauka a kanka" Farouq yayi dukka wannan gulmar cikin zuciyarsa yana duban fu'ad dake zaune yana kurbar maca and ginseng tea. Kaman baiso yake daga cup din zuwa bakinsa,shi kansa,ranshi a jagule,baiso irin wannan yanayin ya tasammasa a irin wannan lokacin ba sam,saidai koma meye zaya faru bayajin zai yarda koda da wasa ya hada jikinsa da ita. Jikin da akullum ya kalla sai yayita lissafin adadin maza nawa ne suka rabeshi?,adadin maza nawa ne suka tabashi?,dame dame sukayi da ita?. Yana da bala'in qyanqyami na fitar hankali,wannan qyanqyamin ya sanya bayajin shikam ko mata biyu zai iya aura,gwara ya tattara mutuntakarsa a muhalli daya. Uwa uba wani irin kishi ne dashi,ba kuma wai yanzu ba,tun tale tale zai iya cewa da kishin ya tashi,dashi aka halicceshi. Baisan maruka nawa yasha daga hannun maamah ba sanda take kawo maza gidan abokan kasuwancinta da suke siyan shaddodin da ta soma business dinsu ba,baisan adadin yawan dukan da yasha a kansu ba......saboda muddin zaka sanya qafarka a gidansu,to shi kuwa zai kafe ya cake a qofa ya hanaka qarasawa ciki. "Babanmu baya so......ya hana maza shigar masa gida,ka koma ka aiko qanwarka ko yayarka" Wadannan sune lafuzzansa a yayin da fuskarsa kan cika da wani irin fushi da zafin zuciya. Kusan baki suke sakewa,kusan duka duka shekarunsa a sannan ba zasu wuce goma sha daya ba,amma zuciyar manya gareshi,zuciyar data kubuta daga dukkanin tsoro saboda kare martaba da haqqin mahaifinsa. Wani lokacin idan ta jawoshi ta daka ta daka,abbansa dake daki kwance yana jiyya shi zaita kiransa,shi zai lallasheshi,yakan ce "Komai na duniya me wucewa ne me babban suna.....komai kuma haquri ne yake zama silar cin nasararsa......ka daina bari ana tabamin lafiyarka me tsadar nan kaji?" Sau tari duk kalan dukan da zata masan ba kasafai ya fiya kuka ba,duk da cewa duka ne ba kadan ba,wani lokaci harda abinda bai kamata ayi dukan ba. Idanunsa saidai suyi jajir,yayita hadiyar yawu da wani irin tsauri "Abba......gidanka ne fa,ta yaya kana kwance zasu dinga tsallakowa suna shigo maka?" Murmushi yakan yi,duk da yakan tsinci ciwo cikin murmushin nasa "Watarana sai labari me babban suna". Ire iren wadannan hirarrakin da abbansa har yau ya kasa sabawa da tunasu,har yau ya kasa jin Normal ne a rayuwarsa,har yau kansa baya iya jure tunasu,duk sanda sukazo masa sai yaji kaman kansa zai tarwatse,sai ya sakejin wani abu yana sanya nisa me tarin yawa tsakaninsa da maamah din,yakan ji kaman bazai iya qara idanu ya kalleta ko ya mutuntata ba......amma ta wani fannin.........uwa data cancanci a kirata mahaifiya irin ameenatu anni......itace ke riqo da hannunsu a ko yaushe,ta kuma qarfafesu da yi mata biyayya. Rana daya daya fahimci ta fara sana'ar dalilin aure,adadin maza da matan dake kai kawo a gidan suka dadu,a ranar ya yiwa wani mummunan rotsen da da qyara aka kashe maganar a police station. Ranar nisan kwana ne kadai ya kawoshi yau da ake magana,don ta sakashi a daki ne ta masa wani irin duka da sai da ya daina numfashi,tun abban nasu dake daga kwance ba daman tashi ya ceceshi yana kiran sunanta gami da qoqarin dakatar da ita,har yawun bakinsa ya dauke tsaf,yayi shuru ya zubawa sarautar Allah ido,yana jin sautin dukan da maganganunta,amma baya iya jin koda tarin muhammad. Yasan halinsa.....sha wuya ne dake iya shanye zafi da tsananin duka,yasan kowanne irin nau'in azaba take masa bazaiyi magana ba. "Me shegen baqin hali irin na ubansa.......baka isa ka hanani neman kudi ba wallahi,yadda talauci ke neman kai ubanka ramin qabarinsa tun lokacinsa baiyi ba......ni bazan zauna talaucin yayi ajalina ba". Qarshe dai musaddiq ya aika ya dinga zuba masa ruwa kafin ya farfado. Ta dauka zai rusuna daga ranar,amma sai taga kaman ma bashi ta daka ba,sai ya canza sabon salon kora da hali wajen yayyanka musu takalmi,karta mota da sace tayoyin motar ko na babur.......still marasa haquri a cikinsu police station suka.kaishi da qyar ta karboshi,zuciyarsa kuma na a tsaye bai rusuna ba,dolen dole ta tattara ta canza sana'a,waccan din saidai tayi a wani wajen daban amma ba cikin gidansu ba. Ajiye roban maca root din dana ginseng farouq yayi yana kallonsa. "Amma yallabai......wadannan abubuwan biyu kaman suna enhancing libido fa.....and..... ". Wani kallo fu'ad ya watsa masa da idanunshi da sukayi laushi qwarai,ya miqa hannu yana fusge container din ya ajiye a gabansa "Baka lura kuma yana boosting energy ba?" Ya fada cikin jin haushi. Dariya sosai ya qunshe farouq din yana gyada kai kaman qadangare "Yes.....yes na gani,kaman kai kenan da kayi loosing energy dinka ko?.....wannan bazai boosta maka komai ba dude.......you need a......." "Zip it" Ya katseshi da kakkausan kallon nan nasa. Shikam farouq bai gama maganansa ba,baiga abinda zai sanya a hanashi fadin abinda yai niyya ba,sai ya janye baya yana daga kafadu. "Duk wani abu da zai maidaka namijin gaske you're Comsumpting......but ka kasa kunna engine din kadan......" Bai qarasa ba ya cire spoon din cikin mug din ya jefeshi dashi,abinda ya sanyashi kasa qarasa maganan......amma kuma ya kece da dariya,wanda shigowar anni parlor din ya dakatar dashi daga dariyar. "Farouqu.....zoka miqawa muhammadu ya dubamin wannan address din.........wata qawata ce muna magana dazu ashe sun shigo suma". Karbar address din yayi ya kalla,bai gane gurin ba don haka ya miqawa fu'ad. "Few kilometers ne tsakaninmu,zaki je ne anni?" Ya tambaya yana dubanta. "Eh amma sai wajen gobe nake tunani.....tunda yau kaman naji amna tana fadan inda zasuje,ba zaa bar gidan ba kowa ba duk da ba wani abu bane". Kai ya jinjina ya ajiye takardar,sannan ya daga mug dinsa yana shanye ginseng tea dinsa abinsa,ba tare da ya maida kai ga kallon da farouq yaketa binsa dashi ba. Dukkaninsu farouq ya xuba a mota suka fice. Sosai suka zaga garin,guraren da sukaje sun kusa biyar,amma duk da haka amna bata gaji ba,fadi takeyi "Ya farouq.....don Allah mu zaga Maldives gaba daya kafin mu tafi,tunda island ne baida girma can can". Dariya musaddiq ya bushe dashi yana kallonta "Kinsan yawan guraren da suke dashi kuwa amnee......a qalla fa gurare dari da tamanin amnee,yaushe zamu iya zagayeshi?" "But......amma please BB,gobe ma ka fita damu,inason naci rihaakuru fish paste.......kifin Maldives please ya musaddiq" Ta fada tana narke murya. "Ki bani cin hanci mana saina roqar mana shi,harda traditional market dinsu.......rannan naga suna saida abubuwan gargajiya sosai.......i assured zakiji dadin gurin" Maganan musaddiq ta sake gigita amnee,ta dinga roqar farouq,har sai data saka sabreen a ciki. "Please BB farouq......a taimaki autan anni mana" Sabreen din ta fada da sassanyar muryarta dake da wani irin nutsuwa. Murmushi farouq ya saki,tana da kima a idanunsa da martaba me yawa,yana ganin mutuncinta sosai saboda yanayin nutsuwarta da kamun kanta. "An gama tunda.matar.oga ta saka baki" Dariya ya basu dukkaninsu har ita sabreen din sai data murmusa kadan. Har yau ya kasa yarda ko sau daya da binciken fu'ad a kanta......baisan meye dalili ba,duk da ya sani shi din mutum ne mara gaggawa akan kowa da komai......amma gaba daya halayensa sun canza a kanta,bazaice kuma ga wani dalili babba guda daya ba. *_DUNIYATA LITTAFIN KUDI NE(PAID BOOK),KAI TSAYE KI TUNTUBI WANNAN NUMBER_* 08187255862 𝐃 𝐔 𝐍 𝐈 𝐘 𝐀 𝐓 𝐀 _Zafafabiyar_ ̶B̶O̶O̶K ̶2 ⱧɄ₲Ʉ₥₳ 𝙋𝘼𝙂𝙀 72 72 Kusan dare ya soma nisa sanda suka isa gida,basu kuma lura da hakan ba sai da suka shiga parlor din gidan suka sameshi zaune saman qananun sofas din dake a falon. Yau idanunsa suna saye cikin farin glass wanda hasken allon system din gabansa ya sake fidda hasken kwalbar glass din. Kallo daya farouq ya masa yasan ta baci,ba kasafai ya fiya amfani da glass din ba sai idan idanunsa suna masa wani iri,don yana zuqe hasken kowanne abun amfani kafin ya samu shiga kai tsaye cikin idanun nasa. Gaba dayansu kowa sum sum ya soma shigewa cikin falon yana dosar qofar dakinsa. Mamaki ya cikata ganin har suka tako veranda din farko na gidan sunata karadi abinsu kuma cike da karsashi......amma da ganin wanzuwarsa kowa ya kama kansa. "Sai da safe" Ta tsinci muryar farouq da shima ya kama kansa zuwa dakinsu,abinda ya sanya jikinta yin laqwas itama ta qara hanzari zuwa nasu dakin ganin kowa ya fashe daga parlor din. A gaggauce ta shige toilet da duka kayan wankanta,tayi wankanta ta kuma shirya a can,tana fitowa kuwa ta nade saman sofa din data kwana jiya akai tana curewa waje daya cikin comforter din data dauke. Bawai sanyi takeji ba ko wani abu,kawai tanason takurawa kanta ne tayi bacci kafin ya shigo. Bata jima da kwanciya ba kuwa taji shigowarsa,ya ajiye komai a muhallinsa ya taka zuwa toilet. Da alwalarsa ya dawo dakin,kamar jiya ya shimfida abun sallah ya fara sallolin da batasan sanda ya gamasu ba,don gajiyar da tayi yau din ya dinga sassauke duk qashin jikinta gajiya tana fita. ★W A S H E G A R I★ K'arfe hudu na yammaci dukkaninsu suna tsaye gaban motar suna qoqarin shiga,saidai gurin ya kaure da hayaniya wanda kusan qananun fada ne da musu tsakanin saddiq da amna wanda dukkaninsu bakinsu baya iya shuru. Tuni Jordan yayi zaune mazaunin driver yana jira su kammala shiga "Anni tayi warning na kaiwa dare......i think wancan hamman naku yakai qararku an fitar masa da mata har dare.....oya guys.....hurry up muje mu dawo" Ya fada yana dan buga seat din motar,abinda ya sanya musaddiq soma shiga yana cewa amna. "Yau zai gane qaramin talaka ne....... Don't argue with him.......shigo auta" Musaddiq ya shiga maganan don ya kawo qarshen fadan. Juyawa amnan tayi ta miqawa sabreen wani baqin kati da yafi kama da atm "Matar oga.....yau ina jakanki.......ga wannan anni tace na baki,naki kudin tsarabar ne da boss ya saka miki kiyi siyayya". Bin card din tayi da kallo,ita bata taba ganin card ma irinsa ba,to amma kuma ita me zatayi da kudinsa?. Ko fitarsu jiya ma ba wani abu ta siya ba,amma duk da haka saida farouq ya cikata da siyayyar da ko budewa ma batayi ba. Hannu tasa ta karba card din kawai,ta daga qafanta tana niyyar shiga motar sautin musaddiq ya sauka a kunnenta "Wow........kallemin guy dincan" Ya fada yana tabo sadiq "Tashin sense" Saddiq ya furta yana kallon fu'ad dake tahowa. Cikin wani irin taku me dan sassarfa,sanye yake da wasu lafiyayyun suspenders da suka sake bayyana ainihin zallar quruciyarsa,suka kuma sake kwashe shekarunsa suka boyesu tas......saika rantse da Allah shi din sa'ansu saddiq ne. Saman kansa homburg hat ce data fidda kyakkyawar fuskarsa da wani irin kwarjini da kwantacenn kyau da zai iya gaya maka lallai shi din ruwa biyu ne da ake kira da halfcast. Sosai kayan suka zauna masa a jikinsa,rigan na dan bayyana muscles din da jikinsa ke dashi,wannan kadai zai gaya maka qaqqarfa kuma ginannen jikin da yake dashi. "Gayennan yana wuta.....anya ba zamu koma ciki mu canza dressing ba......kada maldivians dinnan su dauka age mate dinmu ne fa" Musaddiq ya fada sounding seriously. Dariya sosai amna ta fashe dashi tana dora kanta kafadar saddiq "An gaya muku ya fu'ad wai sa'anku ne?,ku sallama kawai ku huta......idan kanajin babban kifi to shine.......kunga maza kun raina kanku ko?" Dungureta saddiq yayi yana janye jikinsa "Zakiyi dariya da kyau ai......abinda ya kamata ki fara tambaya ko ki damu dashi shine dalilin da yasa ya fito.....ku koma ciki ba zaku je ba,ko ya fito ne mu fita tare kinga yau shikenan......ba sauran sakewa" Tsit dukkansu sukayi,saboda sunsan halinsa zai aikata da gaske. Kowa ya dauke wuta a cikinsu suna fargabar hukuncinsa,har zuwa sanda ya qaraso. Da ido kawai ya yiwa Jordan inkiya ya fito daga mazaunin driver din,ya zagayo kujerar me zaman banza ta kusa da driver ya shiga yana cewa farouq "Shiga mu tafi". Da kallo farouq ya bishi,har ya shiga ya zauna,ya daga idanunsa masu cike da kwarjini ya kalleshi yana daga waje "Ko ba zaka tafi bane ka tsaya kana kallona?" Kai kawai farouq ya kada yana tunanin abinda ya sauya ma fu'ad ra'ayi ya aminta da karan kansa zai bisu. Yau fitar dadinta sai taji baikai na jiya ba tun akan hanya,duk hirarsu suna kiyayewa da hayaniya ko abinda zasu fadi. Hira suke da farouq a gaban mota duk da batajin me suke fada,a haka suka isa guri na farko. Sunyi yawo sosai cikin kasuwannin da suke da kayan gargajiya na al'adun qasar Maldives.....sunyi siyayya kaman ba gobe,duk da bata taba komai daga card din da amna ta bata ba,hasalima a cikin mota ta barshi cikin handbag dinta da bata fito da ita ba. Gurare da yawa idan sunje zamansa yake cikin mota,dama shi din bai damu da shiga gurare irin wadannan ba. Koda sunyi tafiya guraren da yakanje gurare ne da suke da alaqa da kasuwancinsa,ko tarihi na kasuwanci ko kuma zai amfani kasuwancinsa,shi yasa yau din suka cika sosai da mamakin ganin yabi bayansu,duk da dukkaninsu kowa ya ta'allaqa hakan da sabreen ce sila. Guri na qarshe da suka je,suna fitowa ya miqa hannu ya karba key na motar daga hannun jordan "Zaka iya komawa gida" Yace dashi kai tsaye. Takawa yayi a hankali ya isa gaban motar,hannunsa daya zube a aljihun wandonsa,yasa hannu ya bude motar ya shige seat din driver. Junansu suka kalla tsakanin saddiq da musaddiq da amna,mamaki ya cika kowa ganin yau hamma da kansa zaiyi driving?,wani abu da suka jima basu ga yayi ba "Zaku shigo mu tafi ko na wuce abuna?" Ya leqo kansa yana magana dasu da miskilar fuskar nan tasa. Har rige rigen shiga suka dinga yi kowa mamaki kwance qasan zuciyarsa. Kaman yadda kusan komai nasa ya banbamta dana kowa haka tuqinsa,driving yakeyi cikin wata irin qwarewa da nutsuwa,gudu baiyi yawa ba......haka babu laqai laqai. "Ina muka nufa ne sir?" Farouq daya kula ya sauya hanya ya tambayeshi yana kallon fuskarsa dake a dinke tsaf. Shi kwata kwata ma guraren da sukaje kaman basu bashi walwala ba ko kadan. "Siyar daku zanyi na qara jari" Ya amsa masa a taqaice yana sake maida dubansa sosai ga titin. Dariya sosai farouq ya saki yana relaxing jikin kujerar motar "Hakan yayi ai......dadin abun bamu kadai ka debo ba ai" Yayi maganar yana turo p_cap dinsa gaba. Sarai ya gane me yake nufi,shi kuwa bazai kulashi ba,saboda neman wajen da zai dan sake samun relief kawai yakeyi. Sannu a hankali suka shiga Vaadhoo island sunan dake rubuce baro baro a allon sanarwa. Ihu amna keson saki na murna amma sanin wanda ke driving bayason magana me tsauri ko hayaniya ya sanyata danne bakinta ta dole tana duban saddiq dake zaune opposite dinta. Gira ya daga mata alamun tambaya,saita nuna masa map na inda suke ta qaramin screen din dake maqale a gefansu. "Vaadhoo.......glowing island!......sea of stars" Ta fada da wani irin farinciki daya lullbeta don sai a sannan ta lura da sun qaraso glowing island din. "Addana.......mijinki is very incredible wollah.......kinyi dace......kin dace....he's very calm,ya iya surprise,komai nashi unique ne" Ta fada farinciki yana kamata,farincikin yau zata ga inda ruwa yake haske......yashi da qasar gurin itama ke haske tamkar an watsa taurari,wannan yana gaya musu qila ya musu booking na kwana a wannan sabuwar duniya,ko kuma zasu kai dare a wajen suka yadda komai yake gudana. Murmushi kawai tabi amna dashi......babu wani abun burgewa tattare da yayan nata......itace dai bata sani ba. Amma kuma sai itama ta samu kanta da fara sallamawa al'amarin sanda suka isa adhaaran prestige,ma'aikatan wajen kuma suka iso suna maraba dasu,da alama sunsan da zuwansu wajen. Da idanu kawai take bin gurin,da gasken gaske ta zama 'yar qauye tuburan. Gidaje ko dakuna zatace saman ruwa da wani irin tsari me jan hankali. Bata da sauran abunyi illa bayansu da tabi kaman yadda taga sunbi daya daga cikin ma'aikatan saman wani shimfidadden abu daya zama hanya kuma abu daya da zai hanaka tafiya saman ruwan. Kai tsaye zata iya kiransa hotel ko gidan saukan baqi. Suka miqawa kowannensu wani dan card da komai da komai,sai amna ta daga kai ta kalleta bayan ta gama dubawa. "Ga inda zamu zauna can.....zamuci abincin dare a nan.......zami fita sea of stars muyi kallo harmu shiga idan da yiwuwar haka.....komai mukeso zamuje mu karba......amma adda naso kwana zamuyi......inama hamma yace mu kwana?" Amna ta fada tana duban sabreen da hankalinta yake kan ruwan dake gaban door glass din. Shimfidadden ruwa ne iya ganinka wanda yake bada kalan sky blue,abun akwai mamaki yadda mutane keta harkokinsu Kai tsaye suna kai kawo kaman cikin gidajensu suke. "Muje dakinmu adda" Amna ta fada da doki tana yin gaba,bayan ta fidda wayarta ta fara daukan hotuna da videos. Bata yiwa kanta da kanta qoro ba,idanu ta bude sosai tana kallo,yanayin iska da tsarin wajen ya banbanta da duk wani guri data taba zuwa. Gaba daya hankalinta a tashe yake,kaman yadda tunaninta yake a jagule waje daya. Iya zunzurutun dollars din data kashe don tsara komai,tun daga zuwanta Maldives da zamanta a wajen ba wani abu bane na damuwa muddin buqata zata biya. Bahaushe yace ranar biyan buqata rai ba'a bakin komai yake ba. Ya zuwa yanzu da take zaune gaban glass door din tunani ne fal zuciyarta,tana jin kamar tayi wauta da take zaune tana lissafin zai wahala fu'ad din ya tsallake wannan island din ba tare daya shigoshi ba. Tayi zurfi cikin tunanin daya cika mata kwanyarta taji sn daneta daga baya gami da maqaleta da kyau. "You didn't missed your target......you hit it!" Wanda ke maqale a bayanta ta fada da murya me qarfi. A zabure ta cire hannuwanta daga wuyanta gami da waiwayowa gareta,tana jin abun kaman mafarki,idanunta dukka a waje take dubanta "Ki gayan gaskiya.....bazan iya jurewa ba idan kikacemin qarya kike" "Wallahi wallahi me jadda ya shigo......but shi da familynshi ne duka,but kaman dakuna daban daban ne" "Thank god.......ki miqawa wannan Chinese boy din wannan abun.......banason kuskure......after 30minutes zan shiga dakin,ya saka cameran daidai yadda zai nuna komai.......ya tabbatar yayi diluting tablet din a ruwa da lemonsa". "Done!......breaking news zaya fita zuwa ga Nigeria" Ta fada tana barkewa da dariya,yayin da fareeda ta tayata da qaramar dariya mata sauti. Juyawa tayi ta fita,sai ita kuma ta soma zame kayan jikinta da gagggawa tana wucewa wata siririn hanya da zai kaita toilet. Cikin qasa da minti goma ta fito,ta kuma tsaya a side din dressing ta soma balle wasu turaruka tana shafe lungu da saqo na jikinta,ta ware gashin kanta da kyau ta jiqashi da sassanyan qamshin turare,sannan ta bude wani jaka ta zazzage kayan ciki tana dagasu kafin ta fara shirya kanta a cikinsu. Wasu gantalallun riga da wando ne,very skinny,ba iya jeans din ba,har rigar data sanya. Ba wani sirri boyayye ko bayyananne da Allah ya wadatata dashi da bai fito ba walau qashi ko tsoka,me tudu ko me kwari. "Wow......wow" Taji an fada daga bayanta. Kadan ta juya tana kallonta don batasan ta shigo ba. Hannu ta watsa mata tana tambayarta alamun yayi? "Perfect.......kome kamun kan mutum ya ganki sai ya fada......ga kuma wadancan abubuwan na aikinsu yadda ya dace.......zance zaisha banban nan da nan......fatan nasara" Ta fada tana daga mata babban yatsa. Wani shu'umin murmushi ta saki tana takawa gaban madubin,ta sake juyawa sosai a gabansa tana qarewa kanta kallo. Ita kanta ta yaba da kanta ballantana wata halittar d'a namiji?. "Yadda bai sassautawa zuciyata ba bazan sassauta masa ba.......sai na tabbatar na zama cikakkiyar matarsa da shaidu na halas sannan zan barshi ya shaqi numfashi me kyau" Ta qarasa maganar tana daukan chewing gum ta jefa a bakinta tana duban qawartata "Sai na dawo?" Ido ta lumshe sannna ta budesu a kanta. "Inajin inama ace nice yau zan samu nasarar kasancewa da namiji irin muhammad jadda......koda bai aureni ba babbar nasara ce wannan a wajena......best wishes" Wani kallo fareeda ta watsa mata "To mayya........wata miyar ai sai a maqota,babban goro sai magogin qarfe kuma" Dariya ta sheqe da ita "Na sani qawata" Itama saita tayata tana ficewa zuciyarta fes yau din. *_DUNIYATA LITTAFIN KUDI NE(PAID BOOK),KAI TSAYE KI TUNTUBI WANNAN NUMBER_* 08187255862 𝐃 𝐔 𝐍 𝐈 𝐘 𝐀 𝐓 𝐀 _Zafafabiyar_ ̶B̶O̶O̶K ̶2 ⱧɄ₲Ʉ₥₳ 𝙋𝘼𝙂𝙀 73 73 Karo na uku ya sake daukan cup din yana kurban tataccen ruwan strawberry din da shine abu na farko daya soma zaba akai masa. Ya maida cup din ya ajiye yana zare belt din suspenders dinsa. Sosai gurin ya masa kyau ya kuma qawatar dashi,banda annin da suka baro a gida ita daya ba shakka ba abinda xai sakashi qin yanke hukuncin kwana a wajen,amma ko iya hakan ma nan da eleven yasan ya samu refreshment din da yakeso ai. Mamaki ya cikashi jin an murda qofar an kuma shigo,ya waiwaya yana tunanin saddiq ne ko musaddiq,saidai kuma fuskar daya gani tasha banban da fuskokinsu gaba daya. Da kanta ta fito don karbawa amna grilled fish dinta don girmamawa ga yarinyar yadda take kimantata da ganin girmanta,amnan tana da wani irin kirki da sauqin kan da yake bawa sabreen mamaki,don haka tace "Zauna addanki ne zata amso kifin nan da kiketa kwadayi". A gurin ta samu musaddiq shima zai karba nasa order din,wani tsari ne dasu akan grilled fish......zaka je wajen da kanka,zasu nuna maka inda kifayen ki ninqayarsu cikin ruwa ba tare da sanin kwanakinsu qayyadaddu bane,zaka nuna irin kifin da kakeso take a ciroshi a gasa maka a baka ka wuce. Kusan tare suka zaba aka kuma musu irin gashin da sukeso,musaddiq din ya miqa mata daya plate din hannunsa "Addanmu......taimaka ki miqawa hamma wannan please.....kunfi kusa da dakinsa....Allah yasa banyi laifi ba" Murmushi kawai tayi ta karba,tana mamakin yadda suke bata girma haka,bayan duk cikinsu idan ka dauke amna bata girmi kowa ba. Ason ranta tace ya taimaka mata ya qarasa masa dashi,to amma tana jin nauyin kasa masa alfarmar ko don yadda suke daukanta. A nutse take takawa tana duba dakin da take tunanin kamar ya shiga ciki. "Na gaya maka.....kana ganin kaman d wasa nake?......zanci gaba da kasancewa a kowanne taku naka......zan kasance cikin kowanne fitar numfashi da daqiqa naka.......makahon so nake maka.......i can't imagining yadda xan iya ci gaba da rayuwa babu kai". Tayi maganar tana karantar qwayar idanunsa. Tanaso ne komai ya kankama a jikinsa kafin takai ga cikar burinta.......tanason kowanne hankali yayi nesa da tunaninsa kafin ta aiwatar da komai. Wani qaqqarfan yanayi dake taso masa ya sanya ya kasa cewa komai. Kokawa kawai yakeyi da abinda yakeji din,yanason tabbatarwa da ba wannan qaqqarfan abun bane ke qoqarin motsawa?. Yana tsaka da wannan kokawar da duk wani control dake aiki a jikinsa ya tsinci fadowarta jikinsa,ta sanya dukka hannayenta ta masa wata irin bahaguwar runguma kaman zata shige cikinsa tana fadin. Sake kallon number dakin tayi da kyau,ta sake samun tabbacin shine,saita murza handle din tana murmushin hattararta da yadda ta iya gane dakin,ta tura qofan tana sanya qafafunta ciki. "I need you......i need you please jadda......kada ka juyawa zuciyar dake sonka baya.....ka bari na sauke maka abinda kakeji.......kaima kana cikin irin yana yina......na gani a qwayar idanunka" Kalaman da ta fara maraba dasu kenan kafin qwayoyin idanunta su sauka a kansu. Idan idanunta ba qarya sukayi mata ba fareeda khaleed mustapha ce cikin mummunar shiga.......dukka su biyun suna a tsaye,yayin data samu kyakkyawan maxauni a qirjinsa saboda tsahonsa daya shanye nata. "La'ilaha illa anta subhanaka inni kuntu minazzalimeen" Ta fusga daga qasan zuciyarta zuwa labbanta,saidai sautin baikai ga fita a sarari ba ta samu ta janye qafafunta ta koma da baya. Dukka jikinta bari yakeyi,abinda ya sanya plates din guda biyu duka suka kife ruf a qasa. "Sorry madam" Wata murya ta tsarga saman kanta,kafin ta dago ma har ya tsuguna yana kwashe duka plates din. Baya taja kawai ta tsaya tana qoqarin maida numfashinta daidai,don bata da wani qarfi na kwashe barnar da tayi sam. "Relax Sabreen relax mana.....fareeda dince baki sani ba?,ko fareeda dince bakisan yana bibiya ba?,sau nawa kikaga kiranta a wayarshi da luluqin dare?,me kudi ne fa?,yana da kudin da zai iya gayyatar ko wacce mace ta debe masa kewa......that's why aure baya a gabansa......karki yaudari kanki sama da haka ma zaki iya gani...." "And then waye shi a gurinki da zaki rude har haka?" Wannan gigitacciyar tambayar ta fado mata,abinda ya sanyata gayyato duk wata nutsuwa dake kowacce kafa ta jikinta ta azawa ranta tana duban matashin daya miqe yana dubanta da plates din a hannunsa. Cikin harshen turanci ya fara mata magana "Sannu ko?,muje su canza miki wani kifin" Duk da ba'a hayyacinta take ba amma koda ta dubeshi da kyau sai taji a jikinta mutumim africa ne,duk kuwa da cewa shi din ba baqi bane. Duk wani zaren tunaninta ya gama kwancewa,don haka bata da wani zabi illa binsa ta karbowa Sabreen wani kifin,saboda bata da abinda zatace mata idan ta koma dakin haka. Tana biye dashi yana qoqarin janta da hira da mata tambayoyin da bama iya amsa masa takeyi ba saboda yadda zuciyarta ke tsananin gudu. Hannunsa daya ya sanya ya yakice fareedan gefe zuciyarsa tana wani irin mahaukacin bugu. Fushi da feelings gaba daya sun hadu suna neman sauya tsarin bugun zuciya dana numfashinsa. "Wacce irin dabba ce ke?,a hankalinki kike kuwa?" Ya fada da wata irin tsawa data kusa tarwatsa duk wani plan nata......amma data tuna wannan shine plan dinta na qarshe saita miqe da hanzari tana cewa "Bazan taba iya qyaleka ba,sonka mahadin bugun numfashina ne....ka soni please.....koda na iya yaun....." Bata samu damar qarasawa ba saboda wani bahagon mari daya dauketa dashi yana huci,sai gata qasa warwas ta zube bayan ta tuntsura ta dawo ta zauna. Huci yake fitarwa sosai yana jin yadda jikinsa ke sake rikicewa "Daga yau ya zama na farko kuma na qarshe da kika sake shiga hanyata ta kowacce fuska.....if not.....zan batar dake ne a banza......idiot kawai mara amfani!" Yana kaiwa nan ya miqa hannunsa ya dauki key din motarsa da wayar dake ajiye tare dashi guri daya,bai kuma tsaya sauraron kukan data saki tana kiran sunansa ba ya sanya kai ya fice. Yana ji a jikinsa ba daidai yake ba,hakanan baya jin zai qara koda minti guda cikin island din ba.......kaman yadda bazai iya tsaiwa nemansu farouq ba,haka ya nufi hanyar barin wajen wani irin fushi yana lasar zuciyarsa. Kaman cikin gizo idanunsa suka sauka a kanta. Tana tsaye suna facing juna ita dashi. Ya miqa mata kifin da aka nadeshi cikin aluminum foil yana sakar mata murmushi. Bata da wani zabi da ya wuce maida masa martani duk da irin abinda takeji qasan ranta. "Thank you" Ta fadi tana juyawa. Taku uku kacal tayi ta tsinceshi a gabanta babu zato ba tsammani. Wani irin zazzafan kallo take tsinta cikin idanunsa.....wani kakkaifan kallo da kaifinsa ya zarce na takobi.....kallon da tsananin bacin rai yake da matuqar tasiri a cikinsa. Kallo ne daya tabata har cikin b'argonta ya aika saqo sassan jikinta,saidai girma da nauyin abinda ta gani qasa da minti biyar cikin dakinsa ya dakushe kowacce razana tata. Nata fushin ne yake tasowa wanda a dazu tsananin razana da tayi ya cakude da firgici ta rasa ainihin abinda takeji sai yanzu. Yatsansa ya daga yana nuna fuskarta,sai kuma ya sanya hannusa ya damqi nata hannun ba tare daya damu da plate din dake hannunta ba,ya finciketa da wata irin sauri daya qure yanayin adadin tafiyarta ta kasa daidaita tafiyarta da tasa,sai hadawa da tayi da sassarfa. Qoqari taketa yi ta qwace hannunta amma ko cikakken motsi ta kasa yi a hannunsa,kaman yadda bai saketa ba haka bai waiwayeta ba,har sai daya dangana da motar. Seat din gaba ya bude ya kuma sanyata a ciki ya rufe,sannan ya zagaya seat din driver ya shiga,ya tayar da motar d wani dan irin zafin nama,yayu reverse ya fusgeta da wani irin gudu na tashin hankali. Dimaucewa tayi gaba daya har sai data sanya tafukan hannayenta ta rufe dukka kunnuwanta. Ta kasa kallon titi ko sau daya saboda yadda jikinta yake gaya mata irin gudun da yakeyi da ita. Tsahon tafiyar mintina ashirin da sukayi bakajin komai sai qarar iska dake son kutse ta cikin window din motar. Birkin da yaja da wani irin qarfi shi ya kusa sakata tintsurowa daga nata seat din. Murfin ya bude ya fita.....ta dauka a nan abun zai tsaya amma sai taga yana zagayowa inda take zaune. Sake bude motar yayi,ya kuma cafko hannunta kamar dazu ya fito da ita,ba tare daya tsaya kulle motar ba yaci gaba da janta har zuwa cikin gidan. Suka ratsa veranda suka wuce parlor suka tuqe zuwa ga bedroom dinsu. Sai da sukakai tsakiyar dakin yaja burki yana sakinta da qarfi,ta turje taja ta tsaya tana haki idanunta a kansa. Haki yake yana nunata da yatsa,yana son yayi magana amma yadda zuciyarsa ke bugawa a jejjere cikin son wuce qa'idarsa ya sanya ya gaza fadin komai. Kaman daga sama ya fusgo kalaman "Da kowanne namiji ma tsayawa kikeyi?,kowanne namiji ma fuska kike bashi?,wacce iri ce ke!,nace wacce iri ce ke?". Wani kalan tashin hankali taji yana sauke mata saman kai,ta runtse idanunta ta kuma budesu lokaci guda fushinta na qara hauhawa.....wanne irin dan rainin hankali ne shi haka?,ta gaji!,takai maqura! "Daga rana irin ta yau ba zaki sake fita daga nan ba har sai randa zamu bar qasar nan.......zakita zama a dakin nan naga ta yadda zakiga wani d'a namijin,waishin kowa ma burgeki yakeyi?,kowa ma son kudinsa kike?" "Eh......kaman yadda kowacce mace take burgeka!.....kaman yadda kake shirya plan ka kama masauki kawai don ka hadu da wata!.......idan kaga namiji yana burgeni to tabbas shi din ba ragowar wasu bane.......ba sauran wata 'ya mace bane......isashen namiji ne da yake da abun bayarwar ba muna maza b......." Tun daga tsakiyar kanta jijiyar dake aike da saqo ta harbawa kwanyarta saqon KINYI KUSKURE!. Da wani irin hautsinannen yanayi ya waiwayo yana fuskantarta bayan kalamanta sun masa shamaki daga fitar daya fara niyyar yi "Me kika ce?......ragowar wasu?......mema kika ce rannan?,bani da abun baki ko?......kina tunanin zan hada jikina dake ne?. Araharki tayi yawa da ko da wasa ban sha'awar kasancewa tare dake,saidai a yau har cikin raina nakeji ya kamata na karbi sadakina......har kuma cikin raina nakeji ya kamata na banbance miki tsakanin ragowar wasu da wadanda suke da abun bayarwa dama wanda basu dashi.....tare da hakan ina me baqinciki da zaki zama mace ta farko da zata karbi budurcin muhammad fuad" Maganarsa taxo qarshe daidai da sanda shima ya kaita qarshe,ya kuma hadeta da bangon daya zama guri na qarshe da zata sanya qafafunta. Hannu daya ya saka ya soma tsinke button din gaban rigarta na sama,yayi wani irin tsalle yana fita daga gaban rigar tata ya fadi saman marble din dakin. Kafin tayi wani yunqurin ya sanya hannu ya tsinke na biyu,na uku ya biyo bayansa a jejjere da wani irin sauri idanunshi na kafe tsakiyar nata. Caraf ta kama yatsunsa tana riqewa da wani irin kalar tashin hankali,ganin button daya ya rage farar vest din dake manne a fatar jikinta ta bayyana. "Kada ke ketamin haddina......kada ka tab......" Kalmar keta haddin data fada ta zafafeshi da kyau,sai yaji kaman ta gama raina masa wayo. Shi daya biya sadaki shi ake kirawa keta haddi?,cikin qasa sa second biyu ya raba rigar da jikinta ya kuma tsinke hannuwan vest din jikinta ya zameta zuwa saman cikinta. A firgice ta nemi dunqulewa waje daya,saidai ya rigata ta hanyar lalubar tafukan hannayenta ya sanya nasa a ciki ya kuma kafesu da bango,har a lokacin cikin idanunta kawai yake kalla,yanason magana amma kowacce kalma ta gagara fita a bakinsa,yanason ya koya mata darasi fiye da yadda take tsammani,yanaso ya kashe bakin nan gaba daya,ta yadda koda da wasa akace mata ta yiwa wani me suna muhammad rashin kunya ba zata fara ba. Tsoron da yake gani a yanzu cikin idanunta ko kadan bai sanya a ransa na gaske bane,yafi kallon hakan da zallar rainin hankai kawai dason kad'ar da hankalinsa. Hannayen nata ya saki da sauri ya riao qugunta d wani irin zazzafan riqo,ya kawo fuskarta saitin tasa kafin yaja da baya yana sanya fuskarsa cikin wuyanta yana sauke mata wani irn numfashi me dumi daya gigitata lokaci guda. Ba ita daya ta gigice ba.....duk wani kwantaccen tsumi dake jikinsa sai daya motsa,ya kamo numfashinsa da qyar sanda ya cusa fuskarsa tsakanin breast dinta. Wani lallausan qamshi dake fita tsakaninsu yaqarasa wargaza lisaafinsa,ya kuma tayar da aikin qwayoyin da yasha ba tare da saninsa ba. Hannunsa ya sanya ya fara murza fatar jikinta,daga kafadarta zuwa yatsun hannunta sannna ya zurasu cikin nasa ya damqesu waje daya. Qafafunsa yaji ba zasu iya daukansa ba,baya so kuma ya rasa qarfinsa ko daya ko yaji wani softness akan hukuncin da zai mata. Yanason ya bata babban darasin da bazata iya gogeshi ba,yanason ya goge duk wani raini da take masa.....sassaucin da yake gwada mata yanason ta fahimci adalci ne irin nasa da ganin damarsa......daga qarshe yanason ya banbance mata karatun maza suna suka tara. Rabata yayi da qasa yana jefata saman gadon. Tayi juyi da zummar kifewa ta sauka a gadon da muryarta da take wani irin shaking "Banaso......nace maka bana so.....ni ba 'yar iska bace" Wani malalacin murmushi ya qwace masa tamkar wanda ya bugu sosai da kayan maye,wanj gefen na zuciyarsa kuma na masa ciwo da kalmarta. Auren nasa ne iskanci?,bayan duk wani yawo data gama yi lungu da saqo?,shi zata rainawa hankali ta nuna batasan komai ba banda ma lallai ta rainashi?,ai ya zama dole ya goge wannan rainin daga rana irin ta yau. "Zaki gane waye dan iskan gaske tsakanina dake" Ya fada yana tarota,yayin da rub da cikin ya zame masa kaman wata sassauqar hanya ta rabata da bra dinta,ya kuma birkitota idanunsa suna sauka akan qirjinta. Kaman an jona masa wuta haka yaji,a lokacin da take sanya duka tafukan hannayenta tana rufe qirjin nata kuka yana qwace mata. Baqinciki yadda ya tsiraitata yana kamata,bata tsira da komai ba sai fatar jikinta,siraran tafukan hannayen nata basu wani rufe abun arziqi a jikinta ba,sai ta fara yunqurin jawo duvet,abinda ya bashi daman kauda hannayen nata ya kuma maye gurbinsu da faffadan qirjinsa. _na gaji,tun safe nake qoqarin hada muku pages dinnan don na burgeku🥹,muje zuwa a gobe in sha Allah_ _wallahi wallahi duk wadda ta fitarmin da pages dinnan bazan iya yafe mata ba,yadda zata daukeshi ta fiddashi ubangiji ya qwace abunda tasha wahala a kansa daga hannunta🥲🥲🥲🥲_ *_DUNIYATA LITTAFIN KUDI NE(PAID BOOK),KAI TSAYE KI TUNTUBI WANNAN NUMBER_* 08187255862 𝐃 𝐔 𝐍 𝐈 𝐘 𝐀 𝐓 𝐀 _Zafafabiyar_ ̶B̶O̶O̶K ̶2 ⱧɄ₲Ʉ₥₳ 𝙋𝘼𝙂𝙀 74 74 Nauyinsa gaba daya ya aza mata,abinda ya sanya numfashinta yin nauyi,yayin da nasa numfashin ya soma qoqarin yin qaura daga gangar jikinsa. Shi daya yasan kalar abinda yaji sanda farar jikinsa ta manne da tudun qirjinta. Karon farko a rayuwarsa da ya taba jin wani abu makamancin wannan.....karon farko da wani abu me kama da wannan ya taba gilmawa rayuwarsa. Baisan yadda zai iya controlling feelings dinsa ba a irin yadda wani magnet yake jansa ba. Hannunsa dukka biyun ya sanya ya riqe kanta cikin tafukan hannayensa yana kallon fuskarta. Idanunsa ya sauka akan pink lips dinta da suka sake zama pink sosai. Magana takeyi da alama amma kunnuwansa basa tantance abinda take fada. Motsasun da takeyi sai suka zame masa kaman wata tsokanarsa takeyi......shauqinsu ya kamashi sosai saboda irin nau'in siraran lips din da yake muradi ne......amma kuma sai wani abu yazo ya tsaye masa a wuya sanda zuciyarsa ta darsa masa "Ko mutum nawa ne suka dora bakinsu akai?" Yana kaiwa qarshen maganar ya dora lips din nata saman nashi,ya kuma lalubo na qasa ya riqeshi gam tsakanin harshensa. Kaman ya samu lollipop haka ya dinga sarrafashi,cike da wani irin zafin zuciya da yakejin yana watsuwa saman qirjinsa. Tun kwanyarsa na darsa mana adadin mazan da suka kai jikinsu da bakinsu wajen da duk hannu da bakinsa zaikai har ya birkice gaba daya. Zuciyarsa tayi wani irin rauni......rauni na baqinciki,bangare daya kuma wani irin zazzafan shauqi na azalzalar zuciyarsa. Komai kwanyarsa sai ya cakude......haduwar abubuwa guda biyu a gangar jikinsa duka lokaci guda,sai ya dinga ji kaman zai zaunce......kaman gangar jikinsa da qwaqwalwarsa ba zasu iya daukan komai ba. "Ka rabu dani......bace banaso......bana so......ka sakeni......ba 'yar iska bace ni" Maganganunta na qarshe kenan da yaji ta furtasu labbanta suna rawa kaman yadda kowanne sashe na jikinta yake rawa,idanunta sun fito sosai sun qara girma kaman yadda wani irin hawaye me dumi ya cikasu fal har ya gaza adanasu suka fara zirarowa. Labbanta qirjinta dama wasu sasassa na jikinta dukka radadi suke mata. Komai yana mata da wani irin zafi da zata iya kiransa na mugunta kai tsaye. Wani mahaukacin tsoronsa tuni ya gauraye jikinta da zuciyarta. Tsoron abinda ta fuskanci yana da niyyar yi.....wani abu guda daya wanda ko a irin mafarkan da mutane keyi ita bata taba mafarkin faruwarsa a kanta ba. "Why?" Ya tambaya da tasa muryar dake rawa kaman wanda kejin sanyi. Ya ware mata idanunsa da farinciki ya koma kaman an diga manja. Labbansa da suka sake zama red sosai shima dukkansu rawa suke,da alama akwai abinda yake da niyyar fada me nauyi daga zuciyarsa amma sunwa lips dinsa girman da lafazin ya kasa fita. "Why?!.....me yasa baki jirani ba?" Ya sake fada wannan karon a gigice sannan kuma a tsawace,kaman mawunyacin zaki. Tsawar tasa ta qara gigitata,ta rasa me ya kamata tayi sai kawai ta saki kuka. "You're just 25yrs old.....me yasa baki jira rana irin na yau ba?,waye da waye ya taba tabaki?.......na rantse sai nayi ajalinsu......saina kashesu!" Ya fada da wata birkitacciyar murya da zata tabbatar maka tabbas ba'a hayyacinsa yake ba......hakanan kuma fushine danqare a zuciyarsa. "Me yasa suka shigamin gona ta?,me yasa kika basu dama?,me yasa?......Bari naji meye sukaji?,bazan qyalesu ba!" Ya fada a zafafe cikin fitar hayyaci yana zamewa kadan daga jikinta tare da rage daidaita tsahon nasu da yayi. Hannunsa ya aza saman cikinta ya kuma fara saukar dashi zuwa qasan mararta. Wani numfashi taja me tsaho har wani rami dake qashin wuyanta yana lobawa ciki. Duk yadda hannayenta ke rawa batasan da sauran ragowar qarfinta ba sai da taji hannunsa a wajen da ba wata halitta data taba bari takai wajen ba,ta yiwa hannunsa mummunan riqo da muryarta dake rarrabewa. "Kk.....kak....karka....yimin haka......kayi haquri please,don Allah". "Ina da abun bakin ai?,baki sani ba?" Ya tambayeta yana dage dukka girarsa akan fuskarta rinannun idanunsa na qara girma. "Nas......na" "Shshsshshh" Ya fada tana dora dogon yatsansa akan lips dinsa yana ci gaba da duban tsakiyar idonta. "Don't tell me kin sani......zakifi ganewa idan kika gani a aikace...." Ya fada lokaci guda yana ture hannunta. "Don All........" Ta sake yunqurin masa magiya.....wannan karon kuka take da gaske,saidai baima barta ta qarasa ba ya maida gurbin maganar tata da cewa "Karkimin magiya ko ki hadani da Allah.......nima dan iskanne......ya kamata nabi sahun sauran ko?......but definitely saikin bambance tsakanina dasu......." Ya fada yana ture hannun nata da gasken gaske wannan karon,ya kuma maqaleshi a inda bata da damar motsawa. Tana jin sanda iska ta qara yawaita a gurin,alamun dake nuna hijabin dake wajen ya yaye. Ta runtse idonta da qarfi tana jin zuciyarta tana tsintstsinkewa gaba daya,wani abune da bata taba imagining ba kaf rayuwarta "Ban taba bawa kowa kaina ba.....ban taba bari ko yatsana an riqe ba.....na rantse maka......ka yarda dani" Ta fadi tana fata da yaqinin ya qyaleta,wanda ko a iya hala ya barta ta tabbata ya gama da ita......ya kalli jikinta yadda ranshi keso ta cikin hasken fararen qwayayen dakin,wadanda suka yiwa dakin qawanya tarwai kaman rana. Wai inji bahaushe yace ko a jikinsa wai an mintsini kakkausa,sam baima fahimci bayaninta ba.....don a sannan ba wannan bane a gabansa.........yanaso ne ya huce duk wani haushinsa a kanta......koda tayi mu'amala da maza million......yanason dasa mata stamp dinsa......wanda zata mutu tana tunawa MUHAMMAD JADDA daban yake da sauran maza,sau daya tak a rayuwarsa yakeson ya aje mata wannan tarihin da zai kasa goguwa a ranta,daga rana irin ta yau bayajin xai iya sake bin hanyar da mazan da basu da adadi suka bi. Randa tace masa baida abun bayarwa......ragowarsu fareeda,tsananin kai zuciya nesa kawai yayi.......a daren yaso yayi mata yadda ba zata sake marmarin bin wani d'a namiji ba.....amma a yau yana jin zai tattara mata duka hukuncin da ko maza dari ta taba bi tabbas sai gabbanta sun gaya mata. Maidata yayi jikinsa gaba daya,ya manneta cikin jikinsa da wani irin tsatstsauran riqo kaman zai ballata. Hatta da bakinta sai daya kasheshi tas ta hanyar sakayashi cikin nasa bakin dake fidda qamshin mint leaves,yadda numfashinsa ke fita da dumi sosai yake ratsa qofofin hancinta yana aikewa qwalqwalwarta wani irin saqo me rikita lissafi,matsanancin tsoro ya shigeta na yadda a yau komai nashi da nata suke gauraya waje daya......yawun bakunansu.......numfashinsu,dumin fatarsu dama laushinta,qamshin jikkunansu na lausasan turarukansu dama komai da komai. Cikin tsakiyar wannan firgicin......tana tsaka da tunanin mafita ta tsinci baqon abu yana wanzuwa a jikinta.......baqon abu mafi gigitarwa da debe hankalin diya mace musamman a sanda bata tsammaceshi ba. Wani irin azaba ta ziyarci kwanyarta irin wadda bata taba ji ba,duk da bakinta toshe yake da nashi amma hakan bai hana wani irin gunji fita daga hancinta da bakinta ba,ba wata kalma data samu daman fita.....amma gunjinta abune da idan kana dab da dakin kana iya tsinkayen motsin fitarsa. Yadda yake samarwa kansa gurbi a hanyar da wani yanayi da yayi masa kama da sabon muhalli sai abun ya gigitashi da wani irin mamaki. Zato yake daga gareshi ne......baiyi yadda ya dace ba,don ko a mafarkan da ya sha yi bai taba darsawa a ranshi zai samu wani abu me kama da sunan budurci watk virginity a tattare da ita ba,don haka ya sake mata dukka qarfinsa ya kuma soma samawa kansa hanya da dukka kuzarinsa zuciya na gaya masa ya fanshe duk wata kebewarta da wani d'a namiji karon farko kuma na qarshe kaman yadda ya tsara hakan ya kasance. Sake gigicewa tayi da kalar azabar da takeji "Ban taba yi ba......ka qyaleni!" Abinda takeson ta fada kenan amma bai bata daman haka ba. Ci gaba yayi da abinda ya saka a gabansa,yana jin wani irin yanayi da bai taba tsintar kansa a ciki ba yana mamayarsa. Yana sake kutsawa yana sake shiga mamakin abinda yaketa taraswa din,wani irin abu yakeji saman kansa me kama da hauka......kowanne hanya da kunnuwansa zasu isar masa da wani sauti har yakai ga kwanyarsa don ta tantance abinda ya dace yayi da wanda bai dace ba.....limit din daya kamata ya tsaya da wanda zai wuce dukka sun toshe,wata duniya daban ya zarce wadda baya ganin komai kuma bayajin komai.......daga shi sai abinda ya sanya a gaba kawai. Komai ya qarasa kwance masa sanda ya tabbatar ya gama bude kowacce hanya ya kuma kai qarshe,ya fara aiwatar da komai da wani irin tsumammen kuzari da bai taba tunanin ya jima haka a ajikinsa ba. A lokacin ne shima komai ya qarasa kwance masa,bakinta da yake rufe dashi ya gagara ci gaba da riqonsa ya sulale yana cusa fuskarsa tsakanin wuyanta da qirjinta. "Hammm.......hammmmmmmmmaaaaaa" Ta samu kanta da fadi da wata lanqwasashiyar murya tana jin kaman mala'ikan mutuwa ne yake saukar mata. "Yaaaaafffff......fffuuuuu......hammmmm" Ta sake hado kalmomin da zummar tsaidashi ko bashi haquri tana ji a ranta wataqila taci nasara ya saurareta,wataqila ya sassauta mata azabar da yake gana mata komai girman laifinta a gurinsa,wataqila ya.mata wannan alfarmar karon farko data taba neman alfarma irin wannan a wajensa.......saidai kuma inaaaa........wani azaba daya ratsa tsakiyarta sai dukka kalaman suka subuce mata,numfashinta kuma ya qwace mata.....duhu ya ziyarci idanuwanta da kwanyarta. Yaji ya kuma ga kaman haruffan sunansa akan labbanta,saidai baisan ainihin abinda bakin nata ya fadi ba. Duk da ya fahimci inda komai ya dosa yana kuma ta qoqarin controlling kansa amma ya kasa.......ya kasa yiwa kansa waigi.......ya gaza tsaida kansa ko saisaita kansa koda na minti daya,bayajin kuma akwai wani abu dake da qarfin daidait nutsuwarsa a daidai irin wannan lokacin. Wani irin sabon kuzari yakeji a jikinsa da bai taba jin irinsa ba.....wani sabon qarfi yakeji tattare dashi,yana jin kaman akwai inda yakeso ya isa,akwai inda yakeso yakai dole dole......kaman idan bai isa wajen ba zai iya mutuwa.......kaman idan bai qarasa muhallin ba akwai wani abu maras kyau da zai iya faruwa dashi,yana jin wani abu can kusa da ransa dama zuciyarsa gaba daya,yana jin yadda yake shawagi cikin wani sarari da baisan iyakar fadinsa ba. Wulgawar wani second cikin tunani da lokacinsa da wani irin gigitaccen yanayi shi ya dawo da hankalinsa jikinsa. Wani irin numfashi me dauke da wani irin sauti kamar numfashinsa yana shirin barin gangar jikinsa ya sauke......saukar numfashin da tafi kamanceceniya da gurnanin zaki,kowacce gaba a jikinsa ta saki ya aza mata dukka qarfinsa wani zazzafan gumi naci gaba da keto masa ta kowanne kafan gashi dake jikinsa. Qin sakinta yayi ko ya raba jikinsa da ita.......yana jin kamar idan ya matsa koda kuwa Inches biyu daga gareta zata bace masa......yana jin ko yaya ya motsa kadan zata iya subuce masa,yana jin kamar motsinsa yana iya sanyashi ya rasata. Wata qaqqarfar runguma yayi mata cikin ni'imtaccen ingarman qirjinsa. Jiqaqqen gumin dake tsakanin sumarta goshinta da wuyanta gaba daya ya dinga gangarowa yana cakuduwa da nasa,scents na turaren jikinsu ya sake zama wani irin me sanyi tsananin jikkunansu. Wani irin ni'imtaccen qamshi yakeji yana tashi daga jikinta.......qamshin daya zamewa hancinsa na daban,irin qamshin da zai iya rantsewa bai taba jin abu me dadi a hanci irinsa ba......all over her body ko ina idan zai iya tunawa wani irin qamshi me laushi yake fitarwa. "Dama haka matan suke?" Ya tambayi kansa yana qiyasta adadin shekarun daya dauka yana zaluntar kansa ta hanyar haramtawa kansa wannan nutsuwar da wannan ni'imtacciyar rayuwar. Tunaninsa kaf ya dawo da baya da baya har zuwa sanda ya fara maidata mallakinsa.....har zuwa sanda ya fara keta gonar tasa. "She's a virgin?" Labbansa suka motsa ya furta a fili saidai can qasan maqoshinsa,tamkar dai yana tsoron fada,tamkar dai yana tsoro kada kowa yaji. Yanajin yadda maqogoransa gaba daya ya soye kaman ba wani sauran yawu daya rage a jikinsa. Wani qaqqarfan abu yaji yana mamayarsa bayan wani irin nauyi da yaji tamkar ya sauka tsakanin qirjinsa zuwa mararsa. Yana jinsa yayi wani irin sakayau tamkar ma idan ya miqe iska zata iya dibansa ta watsar. Wata irin nutsuwa da bai taba cin karo da irinta ba ke ratsashi,kaman sabuwar iska sabuwar rayuwa da kuma sabon ruhi aka bashi. Yana jin wani yanayi na daban na musamman na mamaye ilahirin bargo da jininsa. Idonsa ya runtse da qarfi yana fadin "How did it turn out like this?,what's the story behind this??" Ya sake maimaitawa kaman me tsoron kowa da komai,kaman bayaso kowa yaji fitar sautin daga bakinsa. Kwanyarsa na cakudewa da kalolin tunanuka iri daban daban,negative da positive dukka lokaci guda. Dif!. Kowanne lantarki dake kansa ya dauke ya daina aiki na wasu sakanni kafin kuma a hankali engine din karbo saqo da aikewa ya soma motsawa yana dawowa saitinsa. Fuskarta da yanayin reaction dinta kukanta dukka hade da magiyarta lokacin da yake yunqurin kaiwa bangon da yake muradi.......yadda labbanta suka dinga motsawa.....yadda oily eyes dinnan da bai taba lura da tsananin haskensu da sheqinsu ba irin yau suke jujjuyawa cike da tsoro firgici da razanin kasancewarsu abu guda "Wannan shine tsoron da akan gani idanun kowacce d'iya mace a darenta na farko......ranarta ta farko da zata fara sanin d'a namiji?" Ya tambayi kansa sannan ya amsawa kansa da cewa. *_DUNIYATA LITTAFIN KUDI NE(PAID BOOK),KAI TSAYE KI TUNTUBI WANNAN NUMBER_* 08187255862 𝐃 𝐔 𝐍 𝐈 𝐘 𝐀 𝐓 𝐀 _Zafafabiyar_ ̶B̶O̶O̶K ̶2 ⱧɄ₲Ʉ₥₳ 𝙋𝘼𝙂𝙀 75 75 "Yes...yes" Zamewa yayi daga gareta yana rage mata nauyin daya aza mata. Tafukan hannayensa gaba daya ya sanya yana qoqarin dago fuskarta da sumar kanta ta zame labule a tsakaninsu,fiye da rabin hankalinsa yana kan dukiyar fulaninta da suke wani irin fusgar hankalinsa suke sanyashi jin kaman ya qare rayuwarsa a tsakaninsu ba tare da ya motsa ko ina ba. Hannu ya sanya ya yaye sumar data rufe fuskartata jikinsa gaba daya yana rawa ya kasa samun daidaito. Tari Tarin abubuwa keta kutse cikin tunaninsa suna fara masa tilawa.....tun daga randa furucin farko ya fara hadasu da ita,yanata qoqarin tuna abinda ya soma gaya mata.......yanata qoqarin tuna da wanne harshe yare ko lafazi zaiyi amfani ya fahimtar da ita HAQURI bisa Tarin kalamansa marasa dadi da ma'ana wadanda baisan adadin yawansu ba. Da wata irin martaba kima da darajarta da sukayi masa fadowar bazata cikin tsokar zuciyarsa,suka cakuda da kowanne digon jini dake yawo cikin jikinsa yakai fuskarsa saman tata ya hadesu guri guda,hancinsa ya saitu da kyakkyawan hancinta me tudu da tsaho. "Am.....soo.....amsor....." Yayita qoqarin maimaitawa yana jin wani matsanancin ciwon kai daya saukar masa lokaci daya. Sai ya zame kansa ya saukar dashi a kafadarta yana cusa fuskarsa cikin wuyanta. Yana ji ne kaman ya zama wani irin ragon mutum kuma rarrauna......yana jin kaman kuka yakeso yayi ko zai sake rage nauyin dake cikin zuciyarsa. "Ya akayi na zama haka?,how?" Ya tambayi kansa,kafin kuma a hankali ya dora labbansa saman kunnenta cikin salo na rada. "Can you hear me.....am sorry......i didn't mean to......to" Sai ya kasa qarasawa saboda bugun numfashinsa daya tsaya cak lokacin daya fahimci babu fitar numfashi sam a hancinta. Fuskarsa ya sake kaiwa daidai hancinta,da gaske ba fitar numfashi sam sam a tattare da ita,wani abu da yazo masa a tsananin ba zata ya sanyashi gigicewar da har baisan sanda ya kira sunanta ba "Sabreeeennn" Ya furta yana tashi sosai hannayensa dafe da gadon,saidai kuma danshin da yaji cikin tafin hannunsa ya sanyashi kai idanunsa wajen ba shiri. "Jini?" Ya furta yana sake fidda idanunsa waje,ya fadi kalmar ne kamar me tambayar kansa da kansa,kamar kuma me bawa kansa da kansa tabbaci. Da sauri ya saka hannu yana jawo comforter din da rabin jikinta yake a rufe rabi kuma take kai,take ya saketa don bazai iya kallon yadda lafiyayyen jan jini ke kwance a jikin farin comforter din ba,jikinsa ya dauki rawa gaba daya......kai kace ba shine mamallakin kamfanin diamond da gold dinnan ba.....kai kace ba shine Muhammad jadda dake razana zukatan maza ba......kai kace ba shine dan gwagwarmayar nan ba.....hustler na gaske wanda baisan tsoro bs bare maganan ja da baya....yakan iya sanya qafarsa kan kowanne bigire ko mataki da ake fargaba saka qafa saboda hatsarinsa....yana fafata da koma waye komai hatsarin dake tattare dashi......yau sai gashi labbansa na sama dana qasa suna haduwa ya gaza koda ambatar sunanta. "Me ka aikata haka fuad?,me ka aikata mata?" Ya fadawa kansa da kansa da qarfi yana sanya tafukan hannayensa dukka biyun yana kama kansa da kyau. Sauka yayi daga gadon da gaggawa yana nufan fridge din dake killace a daya daga cikin corner din parlor din ya bude. Sassanyan ruwa ya fiddo,ya dawo saman gadon yana tattarota cikin duvet din da shi kansa yayi bala'in staining sosai ya azata saman cinyarsa. A cikin tafin hannunsa ya zuba ruwan ya soma shafa mata daga fuska zuwa wuyanta. Sau uku kenan yana yin hakan.....amma ba wani motsi da tayi. "Oh my god!...." Ya fada yana wurgar da gorar ruwan ta fadi qasa ta fata tsiyaya. Fuskarsa ya kafa saman nata fuskan,ya riqe hancinta ya kuma bude bakinta ya soma bata iska ta ciki. Mintuna kadan yaji taja wani irin numfashi da ya tsarga mata har tsakiyar cikinta kafin ta fiddoshi,dagawar qirjinta ya alamta masa dawowar numfashinta,sai ya miqe yana duban fuskarta da tayi wani irin jawur idanunta da suke a rufe suka nuna dagawarsu. "Sabrrrrrr" Ya taqaita sunan nata saboda fitar hawaye daga rufaffun idanunta suka kuma gangaro ta gefan kunnenta. "I was wrong to do that......How can i make it right?" Ya fada yana jin hankalinsa na sake tashi. Bay qaunar kuka sam sam sam,musamman kuka na diya mace. Daya daga cikin abinda ya dinga daga masa hankali lokacin quruciya kukan musaddiq......kukan musaddiq a duk dare sanda maamah ta tafi ta barsu.....kukan abbansa sai ya zama abu mafi tsanani da azaba daya taba gani.....wadannan abubuwan suka sanya ya tsani kuka ainun.....duk da yana da tsananin dakiyar nuna bai dameshin ba. Hannunsa ya dora saman goshinta don cire mata gashin daya sake lullube mata goshin,yana jin kowacce kalma ya debo saita qwace daga bakinsa.......yanajin duk duniya ba wata kalma harshe yare ko lafazi da zaiyi daidai da kunnuwanta idan ya fadesu......shi a karan kansa yakejin kamar ba'a qirqiri wata kalma ta ban haquri da ta dace ko zata dace da girman laifinsa ba. Da sauri ya janye hannunsa yana jin yadda fatar jikinta ke fidda wani irin huci kaman yadda jikinsa ke fitarwa "Ya salam.......ya salam......am sorry,i hurt you sabrrr......Am sorry.....i hurt you,I'll do everything possible to make you feel better" Ya fada yana neman yadda zai gyara mata zamanta a jikinsa. Jinginarta a jikinsa jinta take kaman wani nau'in azaba na daban,batasan yadda wata rai zata fahimci yadda takeji ba.....tana jin kamar zata sake suma ne,don numfashinta sam baya kaiwa hunhunta yadda ya kamata. Tanaso ta gaya masa ya janye jikinsa daga nata amma ba wannan bakin,sai kawai kukanta ya qaru akan nada,abinda ya sake hargitsashi kenan. A zahirin gaskiya baisan yadda zaiyi mata ba don baisan yadda akeyi ba,hasalima shi bai taba zama yayi tunanin zuwan rana irin wanna ba a nan gaba a rayuwarsa bare ya nemi ilimin yadda akeyi ba. Jikinsa ya zame yana jin yadda zazzabi ke dafa qasusuwansa......amma tashin hankalin jinin da yake gani daga jikinsa ya dame wannan. Wayarsa ya dauka,sai ya samu kansa da rasa wanda zai kira.....wazai kira?,wa zai gayawa?,yace masa me?. "Farouq" Kawai shine sunan daya fado masa. Bai damu ba da yadda farouq din zai kalli abun.....abinda kawai ya dameshi yadda zai ceci ranta daga ta'addancin daya tabbatar yayi mata. Idan ya daga kai ya kalli inda jinin ke kwance sai yaji ya aikata baqin fasadi ne kawai yau a daren nan,qaramin kisan kai kawai yakeji ya aikata. "Hello......zamu kwana ne....wajen nan fa yayimin,ina tunanin dawowa nida fannah....." "Am at home" Kawai ya fada da wani irin sound da yaja hankalin farouq din. Aje yanayinsa yayi gefe da wasan dake cikin muryarsa ya bawa fuad hankalinsa "Is something wrong?" Ya fada da tsananin kulawa a muryarsa. Sai daya runtse idanunsa sannan ya budesu yana maidasu inda take kwance sannan yace "Yes farouq......a rude nake.....please help.....i don't know what to do" "You are not alone......am here to help,take your time and tell me what's happening?" Farouq ya sake fadi cikin yanayin kwantar da murya. "We had our first night farouq......i caused her serious injury" Ya fada da tsananin nauyin abinda yake fita daga bakin nasa,saidai kuma ya zama dole yayi hakan,don gani yake kaman tana dab da komawa sumanta. Wutace ta daukewa farouq din. Shima maganan ya masa dan nauyi kadan,duk da ya jima da sanin duk wadda zatayi irin wannan karon da fuad din abun bazai zama da sauqi ba. Don ya bashi relief sai yace. "Relax....ina zuwa". Yana sauke wayar daga kunnensa. Murmushi kadan ga qwace masa duk da qasan ransa tausayin adda sabreen ne fal. Yasan za'a fuskanci hakan daga fuad din,duk da tsananin wayewarsa da sanin lunguna da saqo na qasan duniya.....gogewarsa da mmu'amalarsa da kalar mutane daban daban jinsi daban daban......amma yau saboda tsananin kamewarsa da zame kansa daga dukkan wani batu ko sabga data shafi wannan fannin ya rasa yadda zai taimakawa matarsa. A ransa yaji tabbas ciwon ba qarami bane tunda yaji damuwa sosai a muryarsa. Ya jima yana kallon number wayar anni ta qasar yana kwatanta yadda zai kirata ya gaya mata. Wannan din wani training ne nata data musu. Ko.meye nasu idan ya samesu komai nauyinsa bata yarda wani ya fara jibantar matsalarsu ba kafin ita bare a nan din baisan waye zai kira ba,dole ya koma ya shiga sms ya tura mata saqo kaman haka. _"Muhammad yana dakinsa......he needs your assistance"_ yana tura mata ya aje wayar,don bayason ta kira neman qarin bayani don wabillahi baisan ya zai mata shi ba. Tsaiwa cak yayi kuma wani abu yana dawo.masa da baya. "Ya akayi first night yazu musu da hakan if ba virgin bace?" Ya raya maganar a ransa,sai kuma yayi saurin kawar da ita don shi ya jima da qaryata duk wani hasashe na fuad tun ba yau ba. *_DUNIYATA LITTAFIN KUDI NE(PAID BOOK),KAI TSAYE KI TUNTUBI WANNAN NUMBER_* 08187255862 𝐃 𝐔 𝐍 𝐈 𝐘 𝐀 𝐓 𝐀 _Zafafabiyar_ ̶B̶O̶O̶K ̶2 ⱧɄ₲Ʉ₥₳ 𝙋𝘼𝙂𝙀 76 76 Sanda saqon ya iski anni dawowarta gidan kenan,tazo ta samu gidan ba kowa basu dawo ba. Daki ta wuce ta sauya kaya ta dauki wayar tana fitowa parlor da zummar kiransu taji me ya kaisu yin dare bayan tayi warning dinsu kan hakan kafin su tafi?. Jiya sam bataga sukuni ko walwala saman fuskar fuad ba,kuma tana ankare dashi,yadda ya kasa ya tsare a falon,bai koma daki ba sai bayan dawowarsu. Tasan yana da zurfin ciki sosai,ba kasafai ka fiya sani ko gane abinda yake damunsa ba,amma ita din uwace,koda wanne yare sukayi magana su dukkaninsu tana iya fahimtarsu. Shigowar saqon ya dakatar da ita daga qoqarin kiran nasu da takeyi "Wani sabon sakarcin ne kuma haka?" Ta fada tana zama saman kujera da gorar ruwan dake hannunta ganin me saqon farouq ne. Sau biyu tana maimaita saqon,tasan tunda ya fada da gaske fuad na cikin gidan,duk da bataji alamun akwai kowa ba a ciki,amma sai kuma saqon yaja hankalinta. Cikin fargabar kada wani mummunan abu ne ya faru dashi ta ajiye gorar ruwan tana maida hijab din jikinta,ta miqe idanunta kan qofar dakin,ta taka a hankali ta isa qofar. Knocking ta fara yi,knocking din farko ya sauka kunnuwan fuad dake tsugunne gaban gadon yana monitoring numfashinta,gani yakeyi ko yaya ya matsa zai iya sauke idanunsa a kanta ya tarar ba numfashi tattare da ita. "Waye?" Yayi namijin qoqarin tambaya "Anninku ce" Ta fada a nutse. Idonsa ya lumshe ya kuma bude duka lokaci daya yana furta "Rabbi yassir wala'ta'asir.....ya salam sallim" Yana jin kaf rayuwanshi idan ka debe rayuwar da maamah ta jefasu y taba shiga tashin hankali irin na yau ba. Baisan ta yaya zai bari anni ta shigo ta gansu a haka ba duk da zuwa yanzun ya saka Moroccan jallabiyya a jikinsa tun sanda ya kira farouq. Ita dince sam jikinta yaqi tabuwa masa,da yakai hannu kusa da ita sai maga ruwan hawayen dake idanunta yana qaruwa,ba bakin magana sam sam a tare da ita,amma duban data masa guda biyu tal ya karanto wani irin fushi da kyara a tattare da ita. "Ki taimaka please.....ki bari ko riga na saka miki" Wani fusataccem fushi ne ya sauko mata,ya saka mata riga bayan ya gama ketata ya kuma keta haddi da duk wani mutunci nata da take taqama dashi,ta kuma killaceshi tsahon lokaci?. Yadda ta maida idanunta ta kulle ba tare data ko motsa ba ya tabbatar masa bata buqatar ganinsa ne gaba daya,ga anni na tsaye a qofa dole bazai yiwu ya barta tanata jira ba,haka ya doshi qofar can qasan ransa yana fadin "Me yasa kayi haka farouq?" Yana qiyasta da wanne idanu zai daga ya kalli anni?. Fuskarsa kawai ta kalla da yadda ya bude qofar cikin rashin karsashi tasha jinin jikinta. "Kana lafiya?" Ta jefa masa tambayar tana tsareshi da ido. A yau dai ko karen hauka ne ya cijeshi baya jin zai iya kallon idanun anni bare ya mata bayani. Ratsewa yayi gefe da alamun bata hanya. Itama batace komai ba,ta maida dubanta ne daga cikin dakin tana hango iya abinda zata iya gani din wanda carpet ne da dressing mirror kawai take iya gani,sai ta maida dubanta kan fuskarsa da a yau yakejin idanun anni tako ina a kansa da wani irin nauyi. Batace komai ba itama ta ratseshi ta soma takawa cikin dakin,wanda taku biyu kacal tayi shi kuma ya fice yana laluben inda zaije ya aje kayan kunyanshi nesa da annin,saidai a taku na hudu idanunta suka sauka akan Sabreen,jinin dake jajur yayi staining jikin duvet da comforter din ya marabceta,cikin qasa da second uku ta fahimci me ya faru. "Subhanallah" Ta fadi tsigar jikinta yana tashi. Tasan ko meye ya faru a wajen artabu akasha ba kadan ba,ko tayi taurin kai yaje mata da dukka qarfinsa,qarfin da sam sam tsakanin nata da nashi baizo daya ba. "Muhammadu......maida qofar nan ka rufe" Annin ta fada da madaukakin sauti sanda yake dab da bakin qofar parlor din. Cak ya dakata da abinda yakeyi din,ya maida qofar ya kulle kaman yadda anni ta buqata,ya dawo kuma a hankali cikin parlor din yana laluben wajen zama. Gangar jiki duka da zuciya sai yakejin kaman ba tasa ba,zafin zazzabi yana ci gaba da lullubeshi yana raunana jikinsa,saidai yadda kunyar anni ta rufeshi tafi masa nauyi akan zazzabin. A mamakance take isa gaban gadon "Ikon Allah" Tafada qasan ranta,wato ita dake lissafin ganin result ta hanyar dauka jika,ashe karatunma sai yanzu aka farashi?. Sautin muryar anni cikin dakin sai tayi fatan inama qasa zata tsage ta wuce ciki?,yanzun yana da tsaurin idanun kiran ummansa taga barnar da yayi?,wanne irin terere ne wannna yaja musu?,anni fa.....anni,ya manta surukarta ce?,ya manta akwai kunya me girma tsakaninsu?. "Subhanallah......ya salam" Anni ta.maimaita wannan karon a sarari saboda jinin data gani muraran daya wuce wanda ta hanga daba bakin qofa. Dukka jikinta yayi sanyi sosai,ta tabbata babban barna muhammad din yayi. "Sannu......tashi a hankali ki qarasa bandaki" Anni ta fada tana kamata da tsananin takatsantsan ta yadda zafin ciwukan jikinta ba zasu dameta da yawa ba. Wata siririyar qara sabreen din ta saki,qafafunta kuma suka lanqwashe tilas ta koma ta kwanta duk da anni riqe take da ita. Hawaye ne ke fita ta gefen fuskarta,tsananin tausayinta ya kama anni. Bata taba kawowa muhammad xai gwada rashin haquri irin haka ba,dole yarinyar tana buqatar motsawa ta gyara jikinta kafin ma a samu bakin zaren gane iya adadin barnar data afku. Yana daga falon amma.yana iya hangensu saboda a bude anni tabar qofar,uwa uba yana zaune saitin wajen,saidai yayi kaman bashi a wajen. "Muhammadu" Anni ta kirashi kai tsaye,ya amsa yana tasowa. Idanunshi a kanta yana sauraren bayanin anni. "Akwai ruwa me dumi a toilet.......ka kaita ta gyara jikinta tukunna.....ina zuwa" Anni ta fada tana nufar qofa don itama zuwa yanzun kunyar ke neman kayar da ita. Hakan yayi masa,yabi bayan annin ya maida qofar ya murza key,sannna ya tako zuwa ciki yana nade hannun rigarsa. Sai yanxu kwanyarsa ta fara dawowa aiki,bazai kuma saurareta ba zaiyi kaman yadda anni tace,zaiyi yadda ya dace,dom haka yana qarasawa gabanta ya sanya hannu ya dauketa cak kaman jaririya haihuwar yau,ya lullubeta cikin qirjinsa yana wuce toilet din da ita. Yana jin yadda ta damqe hannuwansa da kyau,da alama haushin dake cikin zuciyarta ne takejin kamar riqon tsaurinta a garesa zai sassauta abinda labbanta da bakinta ba zasu iya fada a yanzu ba. Sake yaye mata dukka suturar jikinta yayi,ta sake runtse ido abun yana mata zafi. Cikin wasu mintuna jikinta ya zama bayyananne a wajensa?,yana qare mata kallo haka kanshi tsaye da kaifafan idanunsa da takejinsu a kanta?. "Bazan kalleki ba indai har bakison hakan.....zan kulle idanuna har saikin bani izinin na budesu" Haushi da takaici suka lullubeta,harara takeson jefa masa zazzafa amma bataji idanunta suna a daidai din da zai ga harara tata yadda ya kamata. Banda ya raina mata wayo yana tsare yana qare mata kallo da wani irin yanayi dake qara kashe masa gangar jiki.....amma kuma yana gaya mata zai kulle idanunsa?, daga baya kenan wai anyi sadaka da karuwa ta furta a ranta. Sake dagata yayi cak ba kuma bata lokaci ya sakata cikin bathtub din da anni ta hada ruwa me dumi qwarai. Wahalalliyar qara ta saki da muryarta dake nuna duka qarfinta ya qare. "Ka sakeni....ka cireni a ciki" Ta fada hawaye na layi bibbiyu akan fuskarta. Wani irin narkewa zuciyarsa tayi da tsananin tausayinta da bai taba jin irinsa akan kowacce diya mace ba idan ka cire anni da amna. Saidai ko kafin ma yayi mata yadda tace ta sake masa wani zazzafan cizo a hannunsa dake dafe da tub din. "Ouch!" Ya fada yana runtse idanunsa saboda tsananin cizon data sakar masa. Ware manyan idanunsa dinnan yayi a kanta bayan ya budesu,idanun da bataji komai tsahon xamani zata iya mance memory din daya aje mata a yau. Labbansa ya motsa yana jin zafin zazzabin har cikin idanunsa,to amma yanayin daya sakata a ciki yafi komai da yakeji ciwo. Ya sani ya shigeta ne da duk wani qarfinsa,yana tsammanin samunta budaddiyar hanya ga kowa......sai abun yazo masa a wata irin bazata a sanda bazai iya controlling din kansa ba kuma "I'm truly sorry for the pain I've caused" Ya fada da wani irin calmness cikin muryarsa,sai ya sanya hannu yana cirota daga bathtub din,yana jin bazai juri barinta tana jin abinda takeji din ba......baisan girman pain din ba bare ya kwatantashi,saidai koma meye ya tabbatar radadinsa ya wuce wasa. Bedside drawer ta isa tsigar jikinta na sake tashi gana girgiza kai da jinjina barnar data tabbatar ba qarama yayi ba,wayarta ta dauka ta duba last call dinta. Qawarta da suka rabu dazu hajja saudat ta kira. "Kuna da wata gynecologist ne mace da zata iya home service kuwa?" Anni ta tambayeta kai tsaye. "Eh akwai.....'yar qasar syria ce.....tana da kirki sosai fadwa haleem". "Na gode.....kimin magana da ita please,ki bata address na gidana.....if possible tunda bamu da nisa kada ta wuce one hour" "In sha Allah kusa muke ai" "Na gode" Anni ta fada tana katse kiran. Farouq ta koma kira,saidai kira har biyu bai daga ba,sai ana ukun sannan ya daga yana sosa kai. "Ku kwana a can,ku biyasu kudin kwana daya.....but kakaimin amna gidan saudat acan nakeso ita din ta kwana" "Okay.....in sha Allah" Farouq ya amsa shima yana jin dadin hakanma da tace,don shi kansa a yanzu ji yake ya zama surukinta,ina ga fuad din. Yadai tabbatar ba zasu qarke lafiya ba idan ya dawo hayyacinsa,to amma wa suke dashi sama da anni?,itace qawarsu abokiyarsu kuma. _uhmmmm....tofa,sabreen naga kin dauki zafi da yawa😄😄.....amma dai muje zuwa_ *_DUNIYATA LITTAFIN KUDI NE(PAID BOOK),KAI TSAYE KI TUNTUBI WANNAN NUMBER_* 08187255862 𝐃 𝐔 𝐍 𝐈 𝐘 𝐀 𝐓 𝐀 _Zafafabiyar_ ̶B̶O̶O̶K ̶2 ⱧɄ₲Ʉ₥₳ 𝙋𝘼𝙂𝙀 77 77 Da wani irin yanayi yake wanke mata kowanne sashe na jikinta da ruwan shower gel din. Wani kuka take saki kawai tana ji har a ranta ya gama da ita,bata da wani sauran qarfi da zata dakatar dashi ko guda daya,cizo kam ta masa shi har batasan adadi ba,amma ko a fuska baya nuna mata yaji zafinsa bare akai ga dakatawa da abinda yakeyi,tamkar ma ba jikinsa take ciza ba,idan ta saka bakinta ma tsaiwa yakeyi har sai ta cire don kanta. Shi kadai yasan me yake sake ji cikin jikinsa,ji yakeyi kaman baiyi komai bama,wani sabon feeling ke taso masa saboda santsin shower gel din dake sassan hannuwansa wanda da tafin hannu kawai yake dauraye mata jikin ba tare daya nema loofah ba. Kafin ya gama wanketa launin idanunshi sun sake canzawa sosai,numfashinsa yana masa nauyi tsakanin qirjinsa da hunhunsa,inda zai samu....inda zai yuwu yana buqatar sake kasancewa tare da ita ko yaya ne.....koda na mintuna kadanne,amma shi kansa yasan yadda take a yanzu dole tana buqatar medical care. Bai taba jin ya zama addicted to wani abu ba irin wannan abun,cikin qasa da wasu awanni qalilan yana jin kamar an halicci abunne sabodashi shi kadai. Hannunsa ya sanya ya riqo qugunta bayan ya fiddota daga bathtub din. Idanunta yake kalla sosai wadanda suka rine saboda azabar kuka. Taqi kallonsa ta kuma sanya duka hannuwanta biyu tana turashi baya,amma ko motsi baiyi ba bare tasa ran zai matsa. Yadda takejin dumin fitar numfashinsa a rarrabe yana sake dasa mata matsanancin tsoronsa,shigen wannan yanayin taji daga gareshi dazu,a yanzun idan yace zai maimaita abinda yayi dazun ta tabbatar saidai ta taqaitawa kanta wahala kawai tayi sallama da duniya......ita kadai tasan abinda takeji,ita kadai tasan radadin da takeji yana ratsata a duk wani motsi da zatayi. "Sabrrrrr....." Ya fada da sautin dake kama da rad'a,wani irin narkakken sauti dake da amo na can qasan maqoshi,idanunsa cike fal da wata irin mahaukaciyar soyayya da baiyi zaton cikin zuciyar tasa akwai wani space daya ragewa wata halitta ba. Kanta ta dauke gefe,maganganu takeson gasa masa amma tana jin idan ta tsaya ta maida masa koda kalma daya ma yana da wannan darajar ashe?. "Sabreeennn" Wannan karon ya kira sunanta full da wani irin sassanyan kuma kwantaccen sauti. Idonta ta lumshe tana mamakin jin sunan yau radam saman bakinsa,kiran sunansa a bakinsa daban yake da yadda kowa ke kiranta,kaman yadda komai nashi yake daban haka furucin sunanta a bakinsa.....amma kuma zuciyarta saita ture hakan,haushinsa ya taso ya maye gurbin wannan. "I know.....nayi abubuwa masu yawa......na bata miki rai da yawa......na gaya miki maganganu masu yawa......i hurt you.....i really hurt you even...." Sai ya kasa qarasawa saboda yadda zuciyarsa take rauni. "Na bata miki da yawa.....na sani,but dukan abinda nayi shine akan hujja da evidence da binciken da nayi wanda yazo da negative reviews......sabrrrr" Ya sake kiranta a karo na uku yana sake zube qwayoyin idanunsa dake cike da shauqi a kanta,yana jin kamar ya dauketa ya bude qirjinsa ya boyeta,yana jin kamar ya hadiyeta ya huta da abinda yakeji qasan zuciyarsa. Ganin da gaske ba zata kalleshi ba sai ya sanya hannu qasan habarta yana juyo da fuskarta. A zafafe ta qwace tana hadiye kukan daya taso mata,ba abinda take muradi a yanzun irin ya sake mata qugunta tayi nesa dashi,ya gama kalle komai da komai nata.....wannan laifin nasa batasan yadda zata gogeshi ba. Sake kamo fuskar yayi ta qwace,sai kawo ya jawota cikin jikinsa ya mata wata kyakkyawar runguma. A karo na biyu fatar jikinsu ta sake haduwa guri daya,wani qaton numfashi ya qwace mata,kaman yadda qaramin yaron da yasha kuka kan saki ajiyar zuciya sanda ya samu kyakkyawar runguma da lallashi daga wajen mamansa. "My heartfelt apologies" Ya sake fada da wani sassanyan sauti me tada tsigar jiki yana miqa hannu ya sake musu ruwa saman kansu shi da ita. Saukar ruwan ya sake tayar masa da abinda yakeji ninkin na dazu,abinda ya qarasa gigitashi kenan,ya dagata yana hadeta da bangon toilet din,ya fara abubuwan da yasan zai samu sauqi da sassaucin abinda yakeji. Wani irin tsoro ne ya sake kamata,takaici da baqincikin yadda yake sarrafa jikinta yadda yaga dama,sai ta sake sakin kuka me sauti tana sake tureshi dakai masa duka da siraran tafin hannunsa. Ba abinda yaji saiji da yayi ma kaman tana sake zugashi,sautin kukanta kawai yake iya ji daya sake zame masa kaman zuga zugi,don sai ya dinga jin kaman kukan wani abu daban takeyi bana baqinciki ba,deep inside yasan na baqinciki ne,but bazai iya qyaleta ba ko yaya......yana buqatar samun sassauci koda baiyi me gaba daya ba,yanajin zuciyarsa da rayuwarsa tana sake mannuwa da ita,yana jin kamar duk wani fitar numfashinsa ya ta'allaqa da ita ne. Sai daya tabbatar ya samu nutsuwar da yake da buqata sannan ya jata jikinsa yana fitar d wani zazzafan numfashi,ya gama kashe mata jiki da tsoro itama,dole ta jingina da jikin nasa tana jin yadda zukatansu ke wani irin gudu,musamman shi da bugun zuciyarsa ke shiga cikin kunnenta sosai saboda kan nata dake kwance a qirjinsa. Duk da ruwan dake zuba saman kansu yana kwaranyewa a sassan jikinsu gaba daya amma hakan bai hanashi tantance dumin hawayenta saman fatar jikinsa ba. Ya gaza bude idanunsa,sau hannunsa guda daya yake shafar sassalkan gashinta daya watsu har gadon bayanta,ya kuma manne sosai saboda ruwan dake zuba "Am sorry......I'm genuinely sorry,My apologies from the bottom of my heart" Ya fada yana kissing goshinta softly. Ture fuskarsa tayi tana sake qayyade adadin rashin imaninsa......tadai san saboda itace kawai ya gwada mata wannan rashin tausayin,banda haka ta tabbatar inda duka mata haka sukeji ba abinda zai sanya su zauna ko suci gaba da yin aure. "Leave me" Ta fada tana qoqarin tashi daga jikinsa. Hannunsa ya sanya ya damqota sosai yana cewa "I can't......ko mutuwa bata isa ya rabani dake ba sabrrrrrr.....zan yita baki haquri har ranar da numfashina ya fita daga gangar jikina......zanta baki haquri ko sau dubu a rana kikeso.....karki wahalar damu gaba daya ta hanyar cewa na barki ko na nisanceki.....don wallahi wallahi wallahi bazan iya ba......i can't do it" Ya qarasa fada yana sake matseta jikin bango sosai sannan ya fara tsarkake jikinsa idanunsa a kanta. So yake qarfi da yaji sai ya cire kowacce kunya daga idanunta,tsaiwarsa haka a gabanta tana jin shine abu mafi girma firgici da razani da suka taba gani. Cikin mintuna kadan ya gama ya kashe shower din,ya jawo babban towel ya wareshi. Ta dauka zai rufa ne ko ita ya bata daman rufawa.....maimakon haka sai ya jawota jikinsa ya bude towel din ya nadesu su biyun a ciki. Shi da ita ba wanda numfashinsa baiso yin qaura ba saboda yadda jikinsu ya sake gauraya dana juna "Shshshsh" Ya fada yana qoqarin daidaita numfashinsa,don bayason tace komai,hannunsa ya sanya a gadon bayanta ya matseta cikin jikinsa gami da rabata da qasa kaman yadda zaka rungumi yaro a haka suka fita a toilet din. Batasan da gangan yayi ba?,oho.....amma gaba daya suka zube a gadon yana fadawa samanta. Ya aje mata nauyinsa sosai har sai da numfashinta ya fara nauyi "Oh....sorry" Ya furta yana dagata gami da bar mata towel din a tare da ita. Rintse ido tayi tana qin dubansa,bai damu ba ya jawo boxer dinsa dake yashe a gefe tun dazun ya saka,ya sanya hannu ya sauketa zuwa sofa bed ya fara tattare comforter da bedsheets din harma da pillow case din,don bayason anni ta sake dawowa idanunta su gani. Toilet ya koma ya shiga sheqa musu ruwa,jikinsa yayi wani irin sanyi ganin yadda ruwan ke wanko jinin. Da gaske ya shigeta ne da tabbaci da yaqinin ta riga ta saba......ya kuma samu qofar a kulle gam....dole taji ciwo koma wanne iri akace masa taji. A yadda yakejin cikakkiyar lafiya a jikinsa ya sani,koda bazawara ce yaje mata da irin yanayin jiya lallai saita yabawa aya zaqinta ballantana ita din da take sabon hannu. Luggage dinta ya bude,ya fidda mata kaya bayan ya saka wata sassauqar riga a jikinsa over sized shirt da wandonta. Fara ce qal data dace da black trouser dinsa. Sama sama yake jinsa shima,saidai abinda ke gabansa ya shafe komai. Da rinannun idanunta ta dubeshi sanda ya aje mata kayan,tana so ne ya matsa ya bata waje ta shirya amma bataga alamun xai matsa din ba,hasalima tsaye yake a kanta ya zube duka hannayensa a aljihun wandonsa kaman zai lasheta,ya zube mata nauyayan idanunsan nan yana jin kamar ya buda qirjinsa ya fiddo mata mahaukaciyar soyayyar data sakar masa. "Ka fita zan shirya" Ta fada a taqaice ba tare data kalleshi ba,hannayensa ya fidda daga aljihunsa ya juya a hankali ya fita. Duk yadda taso ta miqe sosai don ta shirya amma hakan ya gagareta,ba zata iya tsaiwa normal kaman kowa ba,abinda ya sanya hawaye yaci gaba da zuba a idanunta,saita dinga jin data sani ta barshi ya taimaka mata,amma kuma batason komai da zai dinga hadata dashi. Da qyar ta lallaba ta saka underwears dinta ta maida rigar,sannan ta lallaba hannun damanta ta kwanta tana ci gaba da fitar da ruwan hawaye. A nutse anni ta murda qofar tana shigowa da sallama,wata kunya ta taso ta lullubeta,saita rufe idanunta tamkar me bacci,tana fata annin taji kaman baccin takeyi ta juya ta barta. "Sannu....." Anni ta fada a hankali da alama ta fahimci ba baccin takeyi ba. "Zaki iya tashi?,doctor zata shigo ta dubaki". Kai kawai ta gyadawa anni ba tare data iya furta komai ba,ta motsa a hankali tana tunanin yadda zata tashi din. Matsawa annin tayi ta kamata a nutse tana cewa "Yi a hankali" Tausayinta yana kama annin. Yanayin yanayine bame dadi ba,iya yau kawai ta fahimci yaron nata yadda jikinsa ke agine hakama komai nasa "Allah ya baki ikon jurewa" Annin ta fada cikin ranta. Sai a yanzu ta fahimci dalilin da yasa yake kaucewa abubuwa da dama,azumin litinin da alhamis akai akai,harma wani lokaci yakanyi azumin annabi dawud,yau yayi gobe ya huta. Wani lokaci takance "Ka dinga hutawa mana me babban suna......ga azumi ga aiki,shi kansa aikin busy din da kake sakawa kanka pressure din tana yawa". Sau tari murmushi kawai yakeyi ko ya kafa mata hujja da *_DUNIYATA LITTAFIN KUDI NE(PAID BOOK),KAI TSAYE KI TUNTUBI WANNAN NUMBER_* 08187255862