💔💔💔💔❤‍🩹❤‍🩹💔💔💔💔 *DA CIWO A ZUCIYATA* 💔💔💔💔❤‍🩹❤‍🩹💔💔💔💔 _MALLAKIN_ *SAJIDA NIJAR* *FREE BOOK NE* 1️⃣ LITATAFAN MARUBUCIYAR Duk karyar kada Yar mahaukaciya Neman na kaina Bani da zabi Bak'a ce Kutkale Makauniya ce Mage Duk nisan jifa Idan ka raina inda kake Dutse Alkalamin kadarata Bani da zabi Dakika Biyar Now *Da CIWO A ZUCIYATA* *Tallah, tallah, tallah* *SECRET DE LA FEMME DU MANGA* _Gidan Kamshi, Sirrin Manyan Mata, nesa tazo kusa,Amarya ,Uwar gida,Ango da mai gida Har ma da yan mata da samari shin kuna sane da cewa HAJIYA FUSAM ta shirya tsaf domin gwangwaje ku da turarakunta masu dankaran kamshi? Tare Kayan gyaram jiki na musamman ,wanda daga nesa kamshin ki kadai ya wadatar ya isar da sakon zuwanki waje,gidan ki kuwa sai ya zam abun kwatance wajen kamshi, kar na cika ku da surutu bara in fara zayyano su_ Farar Humura Bakar Humura Humura special, humura de bain Humura epicé Lait de nuit Parfums désodorisant Parfums rideau et dras Lait de nuit Alkam Kulakcam *Waɗannan kadan ne daga bangaren turaran ruwa* Gagab, sandal flex, Durot, durus, sandal fleur, tafarce, farce, sandal bangui, sandal, hypotonic sandal, al'ut, coktail creation VIP, Gajiji, Mankaji, turaran wutar labule da cafet, Aba malan, boulettes *Munada bangaren gyaran jiki kamar haka:* mai mai saka santsin jiki, mai mai kanshi, Kayan gyaran jiki mai saka fata ta yi santsi da laushi, kayan gyaran jiki mai saka fata ta yi fari, Sabulu mai saka fata ta yi haske, sabulu mai saka fata ta yi santsi, sabulu mai goge yanayin fata, mai wanda baya saka fari mai gyara fata Sayen na gari mai da kudi gida,sai an gwada akan san na kwarai💃💃 Hajiya Fusam na zaune a kasar Niger domin yin magana da ita kai tsaye tuntuɓi wannan number 97 82 44 94 *SECRET DE LA FEMME DU MANGA* Gidan Kamshi, Sirrin Manyan Mata💃💃💃💃💃 Tunda suka yi sallar asubahi suka yi aduo'insu kamar yadda suka saba ita ta koma ta dan kwontar da hakarkarinta, domin dama ta cika dare ne sosai tana bitar karatun jarabawar da zata gabatar a yau din a makaranta wace daga ita in sha Allah kuma sai ta karshe wace sunna yi zasu samu damar fara zuwa asibiti dan kula da mararsa lafiya ko nace koyon aikin jinya kafin su rike makamin kula da marar lafiya........., Yan uwanta kuwa su biyun watau RUKAYA da AISHA sai suka shiga hana habarsu kamar yadda ya zame masu jiki kama daga gurje tafin kafa, wanka da wuri dan gyara fuska da dai sauransu a matsayinsu da matasan yan mata masu ji da kansu da tsarin kyau daidai nasu da kuma iya wanka dan samun cikar burinsu watau birge wanda suka san sunna iya birgewa a hanyarsu ta zuwa ko ta dawowa daga makarantar summa Sai da karfe bakwai ta yi mahaifiyarsu ta dage labule sanye cikin zumbulelen hijabinta wanda ke yi kamar zai tadeta ta fadi ama kuma baya tadetan dan damatsunnan hannayenta ke dauke shi da zarar ta motsa ta fan leka kanta tana kallonsu da dan murmushi ta sake amsa gaisuwarsu sannan ta ce" Oh Allah, ana nan ana fama da hodar ? Ina ita dayar take ban ji motsinta ba bayan tace jarabawa ne da ita yau din?" Firgigit ta farka a barcin da take yi, mundul taundula daga saman shamakakiyar katifarta wace kwonciyar da ta yi a sama ta sake matse katifar sosai ya zamto ta takure sosai katifar dan dama ba wani auki ne da katifar ba gashi kuma ta hayeta ba ko dan juyawan nan Hularta ta laluba ta warto ta kabeta ta dora saman gashinta da bai fi kamu biyu ba dan bata da tsayin gashi sai cika sosai a kanta sannan ta kama ta mike daga zaunen da ta yi da abin magagin barci ta kalli Aisha ta ce" Karfe nawa ne Aishe?" Aisha ta duba yar karamar wayarta ta sanar mata bakwai ta yi, ta dora da fadin" Bamu tasheki ba dan ko takwas saura kika farka ba lati kike yi ba tunda wankan kawai ne kike yi" Ita dai da sauri cikin yannayin halitarta wace kana iya tunanin idan har ta motsa to fa da shasheka zata yi motsin, sai dai abin mamaki jikinta da ya fi shekarunta bai hanna mata motsawa da kaza kaza ba ta yi bayi tana hangen Mamanta na batse mata bokicin da ta ajiye dan jan ruwa a rijiyar gidansu ta duba sabulunta yana nan dan haka da gudu ta fito ta kinkimi ruwan ta yi bayin da shi ta ajiye abinta sannan ta shiga tubewa dan yin wankan A wajen wankan ne kawai ta dan dauki lokaci, dan akoyta kale kalen jiki irin na tsaftar jiki, koda yake sai ta yi anfani da lemun tsami ta darji hamatarta da du wanu lungu na jikinta wanda ke iya daukan gumi har ya bada wani wari daban irin na jikin dan adam bale ita mai tsoka a jiki masha Allah, kafin take yin wankan ta fito cikin sauri ta yi dakinsu ta warci uniforme dinta dake saman kujera ta kabe ta shiga zurawa bayan ta saka rigar mamanta da kafcecen pant dinta sannan ta zumbula hijabinta ta sake tsalake yan uwanta da har yanzun basu gama nasu shirin ba tana murmushi ta daga masu hannu da fadin" By sisters, sai mun hade" Rukaya ta dago ta fara zuba idannuwanta a takalman da yar uwar tata ta saka takalma ne yan soso plat sun shamuge abinsu , bayan tana da takalma taki biyu bayansu ama dan yau tana jarabawa abin ya karra kwabewa takalmin kirkima ba zata tsaya ta saka ba haka zata tafi Kai kawai ta girgiza domin ta san ba sauraronta zata yi ba in dai ta wannan fannin ne , ita a nata tsarin rayuwar tun da ta gama fahimtar rayuwarta ta gane me take ciki ta yi waje ta ajiye abubuwan nan gefe , ta riga ta sani ne bata lokaci ne a gareta ita, dan haka ta fi dauko fannin da zai gyarata wanda zata iya birge kanta da kanta da kuma Wa'inda ke tare da ita, shine karatunta da kuma nema cikin tarin rashin gajiyawa da rashin son jikin da Allah ya yi mata a cikin irin nata ni'imomin itama Dari biyu yau aka bata, hakan ya sa take tafe tana sakin murmushi da irin tafiyar nan ta gagawa dan a hasashenta in sha Allah minti ashirin da uku zai sadata da ajinta hakan zai yi mata sauran minti goma sha takwas kafin a shiga aji kennan zata karya abinta kafin ta shige, wanda makarantar ke dan nesa da gidansu kadan ama kuma baya mata nisa dan ita a kafa take tafiyarta ta kuma dawo abinta, yan uwanta ne ke bata mamaki, tasu makarantar ta fi kusa da gida fiye da tata , ama idan ka ga sun yi tafiyar kafa ranar tai masu daren kure ba gaba ba baya sai gyaran ubangiji kawai Cikin saurinta ta karasa wajen aunty mai dambu ta zaro dari biyunta ta mika mata ta sanar mata dambu na saba'in zata maka mata tana ta sakin murmushi tana bin hannun Aunty mai Dambu dake zuba mata da kallo, ta sani ne yau zata kile abinta dan kuwa mai cin na arba'in ya kara talatin ai zai more iya morewa Zama ta yi nan ta wanke hannu ta maida hankali ta ci dambun nan sannan ta sayi ruwa daya ta shanye tasss kafin ta mike tana sauke ajiyar zuciya hadi da sakin murmushi domin hankalinta ya kwonta bata da matsala da cikinta takarda kuwa a je a gabza cen dama ba matsalarta bace , watau karatu Kasancewar ranar jarabawa ce, wa'indama basu cika zuwa makarantar ba, da masu zuwa a lati du sun iso tun kafin a shiga, hakan ya sa makarantar ta cika da wuri inda hankalin daliban du ya kakasu gida gida, domin karara zaka ga halaya uku a tare da daliban mabambanta, Wasu zaka ga hankalinsu Kwonce yake dan sun sani sun dauka sun kuma yi iya kokarinsu sun riga sun sani idan sun shiga ajin nan da izinin Allah ba zasu fito a tutar babu ba, watau ko yayane zasu dauki na dauka ko su cinye baki daya Wasun zaka ga sunna ta fama da bude litafi sunna ta bitar abinda ba zai zauna masu a kai ba, saima ya zubar da dan wanda suka cika dare sunna dauka domin dama basu cika leka litafin ba sai irin wannan dama ta samu ta jarabawa, sai ko daidaikun da zaka ga wayarsu ce a hannunsu hankalinsu kwonce, yawanci ya'yan baba da rai ne da suke tunanin tunda babansu ya tara to fa basu da matsala da damun kansu da yin karatu ko faman fafutukar samun takarda , wannan din ba shine a gabansu ba, gidansu an tara a yi sama a yi kasa su kam sun san ko abokin baba ne zai basu aiki a wajen da ya dace da su, shi yasa basu da damuwa a abinda zasu tarar na jarabawar su ci ko su ki ci matsalar wanda ya daurawa kansa matsalar ne, kai hasalima sun zo makarantar ne dan kar a yi masu fada a gida dan iyayensu ne ke so su yi karatun ba wai su ba! Hankali Kwonce ta nufo hanyar ajin nasu, inda yawancin daliban suke, tana tafe tana dan gaisawa da kusan du wanda ta hadu da shi faran faran da murmushinta domin ita dai ba gwali takeda na son birge wani ba, bata kuma zo makaranta dan ta birge wane ko ta bata da wane ba, wannan shiriritar ba da ita ba, to ita batama ga anfanin hakan ba sam, ana ta kai wa yake ta kafa in ba shirmen wasu daliban bama................. "Abokina, ga fa mutuniyar cen tafe, ka ga kamarma sidar hannu ake ko me aka samu da safiyar nan?" Kamal ya fada yana dan murmushin shakiyanci yana kallonta da irin tafiyar da take yi ba abinda ya dadata da kasa , bata da damuwar komai sai ta abinda yake gabanta, wanda hakan abin mamaki ne a wajen samari da yan matan yanzu, duba da irin yadda kowa ke rike da nasa akidar na kin raini, da ɗorawa kai abinda ya fi karfin kai dai da sauransu........... Fuska ya dan gimshe ya kalli inda take zuwan sannan ya maida dubansa kansa fuskarsa a dan gimshe ya ce" Ka fa san bana son haka ko? Na sha fada maka ka mutuntata ko ka shafa mata lafiya, kowa ya yi ta kansa ko?" Zai bashi amsa ta karaso inda suke tsaye fuskarta dauke da madaukakin murmushin gannin ya ji maganarta har ya zo din kamar yadda ta masa maganar jiya da yama da suka rabu daga wajen exercice cewar ya tabata ya zo aji a kan lokaci ya kuma yi exam din nan a cike kar ya saki ya ki zuwa fa? Tsayawa ta yi dan daf da shi ta ce" Bani abin kunnen bawan Allah?" Murmushi ya yi yana fan shafa bayan kansa ya cire abinda ke cikin kunnensa ya mika mata da wayarsa kirar iPhone 11 pr ita kuwa ta kashe ta bude jakarta inda ta san ba zata fashe ba ta saka masa a ciki sannan ta rufe ta sake dubansa ta ce" Ka dauki shafukan fa na fada maka jiyan kuwa?" Shnayayun idannuwansa ya dan bude kamar wani mai shan abin maye bayan babu abinda yake sha haka yannayin idannuwansa suke ya dan kalleta kadan ya kuma gyada kai, shi fa du ba wannam bane a gabansa, abinda yake gabansa aikin da Mahaifinsa ya saka shi yace kuma karfe takwas da rabi ya zamto yana bakin shagonsu na wajen sabon gari dan a sauke kaya a gabansa ya kuma daidaita komai , yau dai wunnin yau sam bashi da wani lokaci gaskiya, shi yasa ya yi safiya ya zo dan baya so su raba hali saboda jarabawar nan, idan dai ta ga ya zo ai ba zata ji haushi ba ko ta yi fadan bai zo ba yana wasa da karatu Da jin dadi ta yi gaba dan duba sunnanta ta barsu ko ci kanka bata cewa Kamal ba, haka shima da ido ya rakata kafin ya dauke kai yana girgiza kansa yana tunanin ta yiwu tun fadan da aka yi ne bata masa magana take masa gaba, bai sani ba cewar ita ba maganar gaba a cikin tsarin rayuwarta ,idan har ta kula cewar zamanta da kai akoy wani abu mai kama da wulakanci ko cin zarafi ne zata janye jikinta cikin salama ba tare da ta yi naci ko ta dorawa kanta abinda zai dameta ba, Hasalima abokin nasu da suke takama da shi shine ya yi mata nacin son kasancewa aboki a wajenta itama, daga wannan bata tunanin akoy wani abu da zai sa ta zamto abokiyar gabarsu, ko fadan da aka yi budurwarsa ce take tunanin meye tsakaninsu haka? Kamal din wajen fada mata bafa soyaya sai ya yi aiki da munanan kalamai da suka sa ta daina gannin kimarsa....., Lalle ita talaka ce, ama a cikinsu ai talakawan da yawa,haka kuma yannayin jikinta ita baya damunta dan ta san Allah ya haliceta haka , haka kuma yake son ganninta, bata tunanin wani bawa zai iya tsayawa ya zageta a duniya dan kawai ita din tana da jiki da ake kiranta da yar lukuta saboda shi, ba kuma ta tunanin bata je neman alfarmar wani wani ba zai wulakantata ba, idan sun kula zumunci ne da zamani yazo da shi tsakanin namiji da mace na abotaka, nata kawancen bai kaucewa tsarin adininta ba domin akida gareta shi kuma yana da addini, layin rayuwarsu ba daya bane dan shi yana zuwa makaranta ne dan yaki da jahilci , dauke kewa, jin dadin mu'amala da jama'a, inda ita kuma take karatu dan samun abin sakawa a baka gobe idan Allah ya nufa!, Ita karatu ne take yi da dukkan karfinta dan bata da madafar da ta wuce bin abinda ya dace dan ta samu rabauta itama da nutsuwar zuciya, shi kuwa wadinnann ya dade a cikinsu domin ya 💔💔💔💔❤‍🩹❤‍🩹💔💔💔💔 *DA CIWO A ZUCIYATA* 💔💔💔💔❤‍🩹❤‍🩹💔💔💔💔 _MALLAKIN_ *SAJIDA NIJAR* *FREE BOOK NE* 2️⃣ LITATAFAN MARUBUCIYAR Duk karyar kada Yar mahaukaciya Neman na kaina Bani da zabi Bak'a ce Kutkale Makauniya ce Mage Duk nisan jifa Idan ka raina inda kake Dutse Alkalamin kadarata Bani da zabi Dakika Biyar Now *Da CIWO A ZUCIYATA* *Tallah, tallah, tallah* *SECRET DE LA FEMME DU MANGA* _Gidan Kamshi, Sirrin Manyan Mata, nesa tazo kusa,Amarya ,Uwar gida,Ango da mai gida Har ma da yan mata da samari shin kuna sane da cewa HAJIYA FUSAM ta shirya tsaf domin gwangwaje ku da turarakunta masu dankaran kamshi? Tare Kayan gyaram jiki na musamman ,wanda daga nesa kamshin ki kadai ya wadatar ya isar da sakon zuwanki waje,gidan ki kuwa sai ya zam abun kwatance wajen kamshi, kar na cika ku da surutu bara in fara zayyano su_ Farar Humura Bakar Humura Humura special, humura de bain Humura epicé Lait de nuit Parfums désodorisant Parfums rideau et dras Lait de nuit Alkam Kulakcam *Waɗannan kadan ne daga bangaren turaran ruwa* Gagab, sandal flex, Durot, durus, sandal fleur, tafarce, farce, sandal bangui, sandal, hypotonic sandal, al'ut, coktail creation VIP, Gajiji, Mankaji, turaran wutar labule da cafet, Aba malan, boulettes *Munada bangaren gyaran jiki kamar haka:* mai mai saka santsin jiki, mai mai kanshi, Kayan gyaran jiki mai saka fata ta yi santsi da laushi, kayan gyaran jiki mai saka fata ta yi fari, Sabulu mai saka fata ta yi haske, sabulu mai saka fata ta yi santsi, sabulu mai goge yanayin fata, mai wanda baya saka fari mai gyara fata Sayen na gari mai da kudi gida,sai an gwada akan san na kwarai💃💃 Hajiya Fusam na zaune a kasar Niger domin yin magana da ita kai tsaye tuntuɓi wannan number 97 82 44 94 *SECRET DE LA FEMME DU MANGA* Gidan Kamshi, Sirrin Manyan Mata💃💃💃💃💃 A lokacin da ta shigo gidan kowa yana nan Bata tsaya tsaye tsaye ba alwallah ta daura kawai ta shige dakinsu ta zauna ta bude litafinta tana yi tana kallon yan uwanta dake hira da makociyarsu wace ta shigo su kuwa sunna tsakar gida da mamansu sunna tataunawa kan shirye shiryen auren y'arta budurwa Aisha ce ta kula da yannayinta domin sosai yannayin nata ke nuni da ranta a bace yake, dan haka da kula ta ce" Hajia sister wai waye ya tabo ki haka?" Kallonta *KAUSAR* ta yi a hankali , sai kuma ta kalli inda mamansu ke fadin maza Rukaya ta fito ta zuba masu abinci su ci Dan sa'ida ta ji a ranta, domin har ga Allah tafiyar da ta yi dambun nan gaba daya kamar bata ci komai ba take ji, du ya yi kasa, dan haka ta kasa ba Aisha amsa har Rukaya ta zubo abincin ta shigo da shi dakin lokaci daya kuma suka mike sunna fita dan Maman ce ta shiga fadan kar su kumkume daki su ci abinci Du a tsakar gidan suka zauna saman tabarma da kwanon da Aisha ta janyo masu ruwan rijiyar ta ajiye sula shiga cin abincin a cikin kwano daya gaba dayansu cikin nutsuwa Ajiyar zuciya makociyar Mama watau maman Naïma ta sauke a ranta tana jin tausayin Maman da ƴaƴanta......., Har ga Allah abin a tausaya ne idan aka yi dubi da yan matan sun fa kai sun kawo ama shiru ko daya ba'a aurar ba, su jira suke yi KAUSAR ta samu miji, wace idan har rayuwarta za'a zauna a duba babu wannan tsarin a cikin tsarin rayuwarta......., Babu wanda zai ce yau ya taba gannin saurayi a matsayin na KAUSAR, yarinyar kamar wata mai bakin aljani ita din da kantama bata da alamun ta damu da wata magana ta d'a namiji a rayuwarta, wani fannin kuwa har ga Allah ana yi mata duba ne na wace bata bada wani dan motsin da zai nuna cewa ta dan itama mace ce tana cikin layin mata a rayuwa ba, ko me yasa ta zabi gabatar da rayuwarta haka? Allah masani Sunna nan zaune har yan matan suka gama cin abincin, cikin gagawa ta shirya ta daura alwallah ta dauki salaya ta saka a jakarta ta kuma daukan hanya domin safe da yama ne jarabawar kwana uku Ta yamar ma bai zo ba haka ta sake shako wani takaicin harda yiwa kanta fadan in sha Allah ba ita babu shi, tunda a zamantakewarsu ba zata iya fada masa magana ya dauka ba, tunda bata isa ta nuna masa mahinmancin karatunsa ya gane me take nufi ba, ita har yanzu ta kasa gane ina ya dosa , in karatun ne baya so ai ba dole ya yi zamansa mana a gidansu? Ama sai ya wani dauko kafa ya zo makaranta ya koma har gashi yanzu ana cikin lokaci mai mahimmanci wanda idan baka samu abin kirki ba to fa ka san me ka shekare kana yi shi bama zai zauna ya yi ba? Tana matukar jin takaicin rashin maida hankalinsa a kan karatu kamar yadda zata iya ji a kan yan kannenta A'isha da Rukaya, bale dai shi da yake biyan makarantar nan mai masifar tsada, ita kanta da ta samu shiga saboda kyan sakamakon jarabawar shigar da takardunta suka yi bata wasa sai shine zai yi wasa? Haka ta yi karatunta bayan sun ci abinci ta shige da wuri ta yi sallah ta yi kwonciyarta domin yau ko abanta ba zai sameta ido biyu ba, haka take idan ana jarabawa bata da lokacin kowa sai an gama Bayan an yi sallar asubahi mamansu na zaune tana jan carbi abansu ya dawo daga masalaci Datijo mai mutunci da daraja, mutun mai karamin hali ama mai wadatar zuci, mutun mai daraja iyali da iyawa talaucinsa a kan muradin iyalinsa na yau da kulun, Abansu mutun ne mai zuciyar nema , yana siyar da turare ne kama daga na feshe har zuwa na haki, yana hi kasuwanni da ma'aikatu da kayan tallarsa ya rabawa masu siya kama daga masu daukan bashi masu biya har zuwa zuwa masu dauka na bakin hanya ciniki yanzu biya yanzu Ya kasance mai saka riba kadan ya saka albarka shi yasa rana ba zata fito dare ya yi bai samu abinda iyalinsa suka ci suka yi yan bukatun yau da gobe na rayuwa, Tukunya dai ukun nan ana dorata a gidansa kofa kuwa ruwan koko za'a dora a yi kari sai an yi shi , basu da mandar abinci bale na ruwa ko na sabulun wanke dati......, Sai kuma Allah ya taimakeshi matarsa macece da ta iyawa talaucinsu Bata da kwatamniyar fade faden abubuwan da suka fi karfinsu bale har ya dawo neme nemen abinda ya fi karfinsa, ta kasance mai talafa masa ce da dukkan hanyar da Allah ya bata dan su ji saukin rayuwa, domin tun daga kan awon masara, hatsi, ko yar shinkafa zuwa sabulun wanka, omo , clean da dai sauransu idan ya kawo ya ajiye har sai ya karro wani da tunanin na gidan ya kai karewa sai ya ga da saura....., Bai taba zuwa gidansa ya tarar da tari tarin abinci banzace a yashe kamar ba nema ake yi ba, bai taba gannin guntatakin sabulai na yawo a cikin gidansa a zubde ba, komai a kilace komai a adane daidai karfinsa, hakan ya sa tafiyarsu cikin rufin asiri da taimakon junna ne, zamansu kuwa bayan Adu'ar gamawa da duniya lafiya sai fatan a je a samu baban rabo gobe kiyama....... Shi dai Abansu bashi da kiba ko kadan, domin lange lange yake kamar zai rabe biyu, mamansu ce mai jiki sosai, dan ifan har jerawa zasu yi ba zaka taba hango abansu ba in ta yi tsaye......a haka tafiyarsu take tafe cikin aminci da tsarin addinin islama, inda Allah ya azurtasu da ya'ya hudu , mata uku dai auta namiji Da salama ya shige dakin ya karasa ya shiga fitar da kwalayan turarukansa yana ajiyewa gefe , ga dakin Mamansu ta kunna dan turaran haki ya gama dakin da kanshi masha Allah Shafa fatihar ta yi sannan ta ciciba ta mike ta karasa wajen kayan da ya zo da su jiya ta dauko ledar da bai mata bayaninta ba ta kawo ta ajiye sannan ta duka tana gaishe shi kamar yadda al'adun malan bahaushe mai nagarta yake Da kula yake amsata da yi mata yan tambayoyin gidan da yaren, itama ta amsa shi sannan ta ce" Aban KAUSAR ledar nan baka min bayani a kanta ba" Ledar ya dan ƙalla yana cirewa yaren turarukan daidaya masu kyau da tsada ya ce" Au na manta, na KAUSAR ne" Dan murmushi ta yi tana kuncewa ta ce" Bara mu ga me yar gatan Abanta ta samu ne?" Shima murmushin ya yi ya dan dakata da aikin da yake yi yana kallonta yana kuma jiyo kiciyar ya'yan nasa a tsakar gida ya san abin kari suke shiryawa da kuma shirin school ya ce" Kayan kwaliya ne jiya a shagin elhaji na ga wata mata na siyawa y'arta, y'ar yadda kika ga Kausar dina ana ta siya mata su nima nace a bani abinda aka basu kin ga takalmin nan mai dan tsayi kuwa? Zai yiwa KAUSAR kyau , harda wata shada nacewa Elhaji a yanka min yafi goma sha takwas karshen wata zan kai kufin mu ci sallah da ita in sha Allah" Mama fuskarta bata gushe da murmurshi kawace a kai ba tana ta dagawa duda abinda take sakawa daban a zuciyarta shine addu'a da fatan gannin wata rana KHAUSARma ta fara gabatar da rayuwa irin ta yan mata, irin yadda mahaifinta ke kokarin nan yana son lalle lalle shima babar yarsa sai ta zamo kamar yan uwantan nan ta san burinsa daya ne Allah ya nuna masa ta samu miji ya aurar da ita ko ya fuskanci kannenta da suke da manema tuntuntuni...., A yanzu dai a kasar hausa shekara ashirin da hudu zuwa da shida ai an kai a shiga dakin miji, sai dai halin rayuwa da kadarar bawa idan har Allah ya yi mijin bai samu ba dole a yi hakuri a yi ta addu'a Tana murmushin ta ce" Allah ya karra budi, ya karra rufa asiri, to ina na yan matana kayan kwaliyar ?" Murmushin ya yi shima ya ce" yan matanki rasawa suke, inace ba'afi sati biyu da suka ce hodarsu ta kare ba har nace da Aisha ni indo hodar nan ko barci za'a shiga fai badata ake yi kau?" Mama na daria ta ce" Kai, ai ƴaƴan nan sunna son kwaliya nu har mamakinsu nake yi, koda yake kwaliyar ai da ranarta gashi du sun samu manema , ama ita hajiar ba ga kwaliyar ba , ba ga dandasa gayun ba, ita dai barta da takarda da byro abinta" Murmushi kawai ya yi , hakan ya sa ta sake tausasar da muryarta, domin abinda ta kwana da shi har ya saka ta kwana tana juyi kennan, maganar ya'yan nasu A tausashe sosai ta ce" Abansu ina so mu tatauna wata magana ni kam" Ajiyewa ya yi ya fuskanceta ya ce" Ai tunda na ga an ki fita a kamawa yayana aiki an bar min yan muleka da shara da wanke wanken asubahi na san da magana, yi bayaninki kai tsaye mamansu" Murmushi ta yi , harshenta na yi mata nauyi kan maganar, a sanyaye ainun ta ce" Baban Muhamadu, kan maganar ya'yan nan ne yan mata...., Abansu dan Allah ina so ka dan duba lamarin nan mu samu mafita, ka ga Aisha da Rukaya sunna da masu so dan manemin auren Aisha yace idanma da hali yana so bayan babar sallah a yi bikinsu dan ya gama ginninsa...., Haka Rukaya a yadfa KAUSAR ta dabar min itama manemin aurenta ya shirya dama yake jira....." Ta dan tsagaita tana sake sada kanta ta ce" Abansu na san menene damuwarka, ama idan har haka Allah ya yi gwara mu fuskanci lamarin a aurar da Wa'inda suka samu malamuncin nasu, kar a tsaya jiran har sai KAUSAR ta samu miji a hade aje Allah ya kiyaye suma su zo ana kame kame...., Ka fa san menene rayuwar y'a mace, gashi KAUSAR bata yin wani kokarin da zai nuna tana son ta samu itama mijin nan ta je ta kilace kanta, yanzu dogon karatun nan na likita dai bana an ga karshensa in sha Allah koda sakamako bai yi kyau ba ba za'a kuma zaman bence ba sai dai a yi jiran wata jarabawar....., Ka ga sai ta zo mu girka sana'a ginaniya mu yi dan karra talafa maka a cikin gidan" Da kyar ta iya kai karshen zancen, domin ta sani ne abinda ke daga masa hankali Kennan a rayuwa irin maganar nan Ya jima yana kallonta , shiru yana tunani Cen ya iya budar bakinsa ya ce" In sha Allah, itama zata samu malamuncinta....., Lamarin rayuwa kowa da irin tsarin da Allah ya yiwa rayuwarsa......, Maganar ta kama sana'a aa ban lamunta ba, tunda dai da sauran karfina kuma ina yin daidai gwargwado bi izinillah zan ci gaba , ba zaku ringa fita sana'a ba, ta cikin gidanama da kike yi dan kar na hanna a ga na so kaina da yawa ne Mamansu, maganar shekarunta kuwa ni baya gabana , ko dan ni na haifa? Lalle yana damuna ama ba shi yake nufin yana gabana ba, abinda yake gabana bara ki ji , dama jira nake yi ta gama, in sha Allah dukkan hanyar da zata dan daidaita rayuwarta zan sake nema na rike, zan kaita a dan kokoya mata dan gyara irin na yan mata, ni bana yiwa y'ata kwadayin auren wane sai dan mutunci ko wanene komai tsufansa, kar ki manta a lokacin da na ganki bakida ko digon kwali a idannuwanki, ina yiwa y'ata fatan miji na gari baki dayansu, dan Allah mamansu ki daina yin magana da sarewa a ciki kin ji? Na san abu ne mai matukar hanna zuciya sukuni, ama idan har ke kika fara haka zaki yi gagawar cin mini kin ji?......, Yaran nan kuwa zan duba maganar auren Allah ya doramu a kan hanya madaidaiciya" Ajiyar zuciya ta sauke tana amsawa da amen sannan ta ciciba ta tashi dan ya ci gana da aikinsa haka kuma yannayinsa baya mata dadi dan walwalar tasa ta ragu, ama ba zata saka damuwar haka a ranta ba, fatanta ya gane ya kuma rike wannan dama, dan idan har suka rayu da jiran babar yarsu in Allah bai yi zata samu da wurin ba sai a zauna a tauye kowa da kowa?, Su Aisha kansu yanzun sun fara gandamewa ai Da wannan ya'yan du suka shirya, ita zata fara fita bayan ta gaisar da Abanta tana ta doka murmushin tambayoyin da yake yi mata tana bashi amsa sannan ya salameta yau har dari uku ya wanka mata hakan ya sa ta fito kanta a sama kamar sarauniya ta zo ta duka ta yiwa Mamanta salama sannan ta mikowa Maman nata watsetsiyar wayar TAUFEEK wace ta saka su Aisha zaro ido sunna kallon wayar domin su sun san cewa ba karamar waya bace, ita dai ce da ba komai ya dameta ba ba wani sannin kudin wayar ta yi bama bale har ta ji tsoron rikewa ta ce" Mama wannan wayar adanawa TAUFEEK ita kar aje ta fashe ina hadeta da kaya a jakar nan" Maman nata ta amsa tana kallonta ta ce" KAUSAR me yasa kika amshi wayarsa har ki je ki yar bakya tsoro? Da gani wayar nan ba karama bace ba fa?" Aisha da ta rafka tagumi ta ce" Mama, wayar nan ai sai ta sayi aunty Kausar tsaf harma a nemi kari, Aunty Kausar da wayar nan kika kwana a gidan nan a san tana nan a shigo a yi kidmashin dinmu?" Rukaya ta yi dariya tana dungure kan Aisha ta ce" Ke haba dai wayar zata wani sayi mutun, ama fa Mama wayar nan ba karamin kudi ne da ita ba gaskiya, koda yake su a gidansu yar autarsuma mai shekara goma sha uku iphone ce a hannunta ranar da muka je din nan amsar books din aunty kamar na kifa kallonsu kawai nake yi, Mamansu wata yar gayu da ita bakinta turanci ya amshe hausar" KAUSAR ta girgiza kai ta ce" Ku dai kula sani, Mama wayar yau kwananta biyu a wajena, ba kin ga irin fadan da na masa da wayar Aba kan karatu ba? To Mama za'a shiga aji na amshe wayar dan karma ya zauna yana dane dane, har an shiga aji kawai ya tashi ya tafi har yau dai da ban ganshi ba, gatanan wayar a hannunki idan ya ga dama ya zo ya amsa, ni ba ni ba shi ko a hanya ya ganni ba zan nuna na sanshi ba, tunda haka ya zabarwa kansa sai ya yi" Ta gama fada da takaici ta mike ta tafi tana fadin ta tafi Aisha a a sake tafa hannu tana rakata da ido kafin ta dawo dubanta kan mamansu ta ce" Iko sai Allah, ni wani lokacin sai su rikitani da tunani, wani lokacin kuma sai kawai in ga kawancen ne kawai, ama yanzun kamar wata budurwarsa????" Rukaya ta ja numfashi ta ce" Ke da ke kadai ce sai a maki maganin haka, ama kuma idan har kika yi duba da yannayin abin nan bayan zumuncin babu komai, aunty fa babu wannan maganar tsakaninta da shi, shima haka, inaga fa shekara hudu ce kawai ya batama, kuma bayan wannan yarinyar da zai aura fa in fada maki komai a hannun Aunty yake, kawai haɗuwar jinni ce mai wuyar fasara, ni abinda ke bani dariya da Aunty idan suka yi fadansu ta ringa rantse rantsen ba ita ba shi, ita dole sai ta sa ya mayar da hankali kan karatun da ya je ko bai je ba takardunsa tuni a hannunsa, kuma ya yi ko bai yi ba sunnansa mai kudi, ama haka ta yi ta fushi shima ya biye mata" Mamansu dai da ta kai wayar ta boye dan ita tsoroma wayar ke bata ta dawo tana fadin" kai maza ku tashi ku yi da jiki ku kama hanyar makaranta ba sai kun yi lati ba ku ce sai an baku na sahu!" 💔💔💔💔❤‍🩹❤‍🩹💔💔💔💔 *DA CIWO A ZUCIYATA* 💔💔💔💔❤‍🩹❤‍🩹💔💔💔💔 _MALLAKIN_ *SAJIDA NIJAR* *FREE BOOK NE* 3️⃣ LITATAFAN MARUBUCIYAR Duk karyar kada Yar mahaukaciya Neman na kaina Bani da zabi Bak'a ce Kutkale Makauniya ce Mage Duk nisan jifa Idan ka raina inda kake Dutse Alkalamin kadarata Bani da zabi Dakika Biyar Now *Da CIWO A ZUCIYATA* *Tallah, tallah, tallah* *SECRET DE LA FEMME DU MANGA* _Gidan Kamshi, Sirrin Manyan Mata, nesa tazo kusa,Amarya ,Uwar gida,Ango da mai gida Har ma da yan mata da samari shin kuna sane da cewa HAJIYA FUSAM ta shirya tsaf domin gwangwaje ku da turarakunta masu dankaran kamshi? Tare Kayan gyaram jiki na musamman ,wanda daga nesa kamshin ki kadai ya wadatar ya isar da sakon zuwanki waje,gidan ki kuwa sai ya zam abun kwatance wajen kamshi, kar na cika ku da surutu bara in fara zayyano su_ Farar Humura Bakar Humura Humura special, humura de bain Humura epicé Lait de nuit Parfums désodorisant Parfums rideau et dras Lait de nuit Alkam Kulakcam *Waɗannan kadan ne daga bangaren turaran ruwa* Gagab, sandal flex, Durot, durus, sandal fleur, tafarce, farce, sandal bangui, sandal, hypotonic sandal, al'ut, coktail creation VIP, Gajiji, Mankaji, turaran wutar labule da cafet, Aba malan, boulettes *Munada bangaren gyaran jiki kamar haka:* mai mai saka santsin jiki, mai mai kanshi, Kayan gyaran jiki mai saka fata ta yi santsi da laushi, kayan gyaran jiki mai saka fata ta yi fari, Sabulu mai saka fata ta yi haske, sabulu mai saka fata ta yi santsi, sabulu mai goge yanayin fata, mai wanda baya saka fari mai gyara fata Sayen na gari mai da kudi gida,sai an gwada akan san na kwarai💃💃 Hajiya Fusam na zaune a kasar Niger domin yin magana da ita kai tsaye tuntuɓi wannan number 97 82 44 94 *SECRET DE LA FEMME DU MANGA* Gidan Kamshi, Sirrin Manyan Mata💃💃💃💃💃 Haka suka mike kowace ta shirya suka fice makaranta, Aisha na ajin karshe a secondary domin ita akoy wasa da karatu, Rukaya kuwa tana karantar malamar makaranta Kwonci tashi har suka gama jarabawa kwana bakwai cif suka shiga hutun sati daya , hakan ya sa hankalinta ta tarkato shi ta mayar hanyar islamiya sai yan shige da fice kasuwa lokaci zuwa lokaci na shorye shiryen auren y'ar makociyarsu da kusan komai ke hannun mahaifiyarsu domin akoy zumunci sosai sannan sun sani ne Mama akoy amana, in dai ka sakata a lamarinka da izinin Allah ba zaka ga ha'inci ba, ƴaƴanta yan mata suka zamto kawayen amarya , ama KAUSAR bata wani yawan shigewa cikinsu, domin haka kawai take jin kanta ba yadda take so a cikinsu ba, hankalinta baya taba kwonciya waje daya idan tana cikinsu, sai ta ga duniyarsu ba daya bane, hangensu ba daya ba, kai komaima sai ta ga ba daya bane da ita da su, hala suma irin lokaci zuwa lokaci da zaka ga sun hade da itan basu da wata sakewar a zo a gani, idanma tana wajen du wani abu na yan mata basa sakata, dan tun daga yannayin jikinta har kafarta bai nuna tana da muradin hakan ba, sai ana gobe daurin auren nema ta yi kunshi a gida, shima Mama ce ta kunsa mata kunshi na hausa hannayenta da kaffaguwanta ta kwana da shi, ya zamto tunda ta tashi sallar asubah ta wanke ta daura alwallah ta shige dakinsu, yau ita daya ne domin kannenta sunna gidan su amaryar cen suka kwana , hakan ya sa da jiki tana gama sallar ta saka doguwar riga kawai ta saka hula ta fito ta shiga aiki ka'in da na'in dan tsaftace gidan domin nan amaryar zata wuni da kawayenta Tana tsakiya da wanke balbalin gidan suka yi salama suka shigo da amaryar da babarsu yayar mahaifinta sai kannenta aka rako amaryar, hakan ya sa ta dakata tana gaishe su da murmushi shinfide a saman fuskarta ta masu jagora har dakinsu inda ta shinfida katifar mamansu ta shinfida zannin gado sabo mai kyau dakin sai kanshin turaren haki yake haka kuma kasan an shinfida tabarma biyu an malale ko'ina, tsaftsaf dai ba dati Tunda ta dage labulen babarsu amaryar ta kama baki tana kare mata kallo, har ta gama ta janyo hijabinta zumbulele ta maka tana sake gaishe su da fada masu su shige ta ci gaba da aikinta har matar ta gama ta fito ta tafi gidan bikin zuciyarta fal mamaki ne ke neman kasheta Lalle Allah ke halita, lalle ta yi mamakin wannan sankacecen sanwon dake bayan Kausar mai sunna duwawu Ashe yarinyar nan hijabin da take sakawa abinda take boyewa a karkashin sa kennan? A kulun sai a rinha cewa KAUSAR balaluwa mai hijab, Kausar bata son kwaliya, bata son meye meye ta ki kama jiki ina zata samu mijin aure wannan zamani na yanzu da mazan suka zamto kyale kyalim shine abinda suke so, gashi Allah ya yankota mai baban jiki sai nuku nuku da hijab kamar zai makata da kasa, ashe ashe rufin asiri ne saka hijab din nan? To da ace Kausar bata lulube jikinta lalle da an ga kudan zumu a tare da ita, domin mazan fa zasu zo ne ko ana ha maza ha mata, tabas da dubu sun mayar da ita doki koda kuwa bata so, kai ita a yau sai ta ga gaskiya gwara da yarinyar ke rufewar, sai dai rufewar ba damuwa bane, damuwar KAUSAR bata damu da gyaran ba, ba wai wari take yi ko wani abin ba, ama a shekarunta bai dace ace tana fita haka ba kwata kwata, yan mashinshinan nan ko na anguwa sun gagara? Da kyar ta kade tunanin a ranta ta shiga harkokin kaye kaye na shagalin biki A ranar an wuni shagulgulan biki, domin anguwarsu anguwa ce ta talakawa ama fa akoy kara, dan ina ana sabga zaka ga kwansu da kwarkwatarsu an hadu ana ta murnar abin, ba wai zaka raba su da tsegumce tsegumcen anguwa ba, ama kuma hakan bai fi karfin zumuncinsu ba, dan kuwa koda irin hakan ya faru akoy Hajia datijuwa wace ta kasance mai tsawatarwa yaren matan , kuma sunna jin maganarta sosai da sosai Kowace budurwa ta sha kwaliyarta ana shan hotuna ama KAUSAR tana fama da rabe raben abinci da sauransu, harta Ankonta bata wani saka ba tana ta kai kawo ne bata zauna ba har yama ta yi aka raka amarya gidansu dan shiryata kafin dare a yi mata rakiya Bayan sallar magariba Mamansu ta shigo tana dan sauri ta shige ciki tana kiran sunnan Kausar Fitowa ta yi tana amsawa hijab dinta a hannunta domin bata jima da gama sallah ba zaune dai take tana karatu Mamansu ta miko mata jakarta ta ce" Ke ba zaki je rakiyar amaryar bane?" KAUSAR ta girgiza kanta tana murmushi ta ce" Mama to wa zai tsare gidan? Yau auta kansa ba dama ba'a ko ganninsa yana cen wajen su Kabir" Mamansu ta yi murmushin itama ta cenza hijab dinta ta fesa dan turare ta ce" Ai kam, to bara na je kin ga sai mun kaita dakinta, ga wayar nan ta wajen Taufik fa kar na fita na barta haka a daki duniya ta rikice ni kuwa su Aisha sun tsoratar da ni da tsadar wayar" Wayar ta dalawa harara tana jin wani takaici nasa ya taso mata ta amsa ta kai ta ajiye dakinsu tana tsaye har mamanta ta tafi sannan ta koma ta ci gaba da karatunta hankali kwonce Bayan sallar isha'i da kamar minti talatin da daya ta fito tana rufe gifan dan zuwa ta kamo Auta, domin ya cika dare haka a waje dan kawai ana taron nan ne da ba haka ba da tuni yana gida sallah kawai yake fita , gashi mamansa bata nan , hakama Babansa gwara ta kamo shi ya dawo gida ya ci abinci ya kwonta ko dan islamiyar safe Dakatawa ta yi ta zubawa galeliyar motar dake parker gaban gidan kadan ido Gane mai motar ya sakata sake bude gidan ta shige, shi kuwa daga zaunen da yake sake zubawa kofar ido ya yi a hankali ya shiga dan lumshe idannuwansa dan maganar sai ta so zame masa biyu a cikin kwonyarsa dan kuwa budurwarsa na magana ne ta wayar da ta yi kiransa da kuma tunanin me nufin komawar aminiyarsa cikin gida bayan ya tabbata ta san motar nan? Jim kadan ta fito tana sake kulle gidan ta karaso hankali kwonce ta bude gaban motar gefen da ba kowa ta shiga ta zauna ta mika hannunta ta dan matso kofar dan a bakin hanya ne ga anguwarsa da yan acaba ......ba komai ya saka ta shiga motarsa ba sai dan ta fada masa abinda ta kulo a zuciyarta! Tarin abinda zata juye masa ne a zuciyarta! Kuma ta rantse sai ta fadawa Taufik duka kaf abinda ta shaka Kasa kasa sosai Taufik dake kallon wayarsa da ta ajiye gaban motar ya ce" Zan yi kiranki *YUMNAH*" YUMNAH dake son sannin wai yaushe zai karaso gidansu ta ce" To shikenan, ama baka fada min karfe nawa zaka karaso ba?" Agogon ya dan kalla, sai kuma kasa kasa ya ce" Zan dai taboki" Wannan karron bai tsaya ta bashi amsa ba ya katse kiran sannan ya juyo yana dan sake rage girman idannuwansa dan ya ga ta gyara zama ta cika fuska tamkar zata fashe ya bata hankalinsa A takaice dai kamar yadda ta saba ne idan ta kwaso masifa sai ta zo juyewa ta rasa ta inda zata fara da kowama hakan ne yanzuma yake neman samunta Da kyar, da kyar ta iya sake cije lebenta sannan ta saka hannunta zata bude motar ta fice Da sauri ya ce" KAUSAR " Dakatawa ta yi ta juyo da wani tuwon takaicin mai hadasa ciwon kai ta sake zuba masa idannuwanta tana sauraronsa Kai ya dan sinne kasa kasa ya ce" Sorry besty " Rai bace ta ce" Taufik, ka rike sorry dinka, nace ka rike Sorry dinka Taufik, bari ka ji in dai ni yar halak ce an haifeni a hanyar halaci ba zan kuma........................." Idon da ya tsura mata da wani irin kallo mai kama da kashedi ya saka ta shiga wani inda inda kamar tana gaban Aba, har sai da ta tuna irin haushin da ya shaka mata sannan ta jure ta yi watsi da wani wasi wasin tunani ta ce" Ba zan kuma yi maka magana a kan harkar karatun nan naka ba, ai da ake fada min nice nale rintse ido dan tunanina na isa ko ina iya gyarawa ne? Ban san cewa nice nake lalube kai karatu ya maka rana ko kar ya yi kansa ne, sai dai na kasa gane a kan me ka zabi zama likita bayan ka san shine aiki mafi hatsari a duniya, domin da allura daya kana iya kashe bawa, na san kana da ilimi, hakan ba yana nufin kai aljani bane, likitanci ba'a cenkarsa sai dai a karanta du ilimin mutun!, Ka ki ka gane ko ka ki ka mayar da hankali zan ce? Duka wannan yanzun kam babu ruwana ka yi yadda kake so Taufik, ka ga tafiata" Watau da ake cewa babu abinda ya fi ciwo a duniya irin ka shako fadanka ka rikoshi da hannu bibiyu irin na rashin mutuncin nan, ka zo dan ka juye shi a kan mai rabo ama ka yi ka yi a maka shiru hakane, watau a ki biye maka hakane, yau ta karra yarda da maganar Du wannan babatun da ta yiwa Taufik, duka kaf wannan fadan da ta saukewa TAUFEEK ita TAUFEEK ya karewa kallo ya mata banza tamkar wata shashasha wace bata san ciwon kanta ba? Ita TAUFEEK ya kyale ta ringa hayaniya kamar zata ari baki? Lallema! Da bacin rai ta maki masa marfin motar , tana juyowa ta ga Auta a tsaye yana bangalar baki shi da abokinsa har yana dage ya ce" Auntynmu, yayanmu ne a motar?" Wani takaici ya kuleta, wai ƴaƴansu, to yau du wani mai kiran TAUFEEK yaya dan yana dan uwanta ta soke!, Da bacin rai ta janyo shi ta ingiza keyarshi gaba bata bashi amsa ba suka karasa kofar gidan ta saka dan makulin ta bude suka shige ko gaishe da Malan Barau bata yi ba domin ya wani kura mata ido har lekawa yake yi motar da ta fito, ta tabata yau sai an dora dandalinta a anguwar Ajiyar zuciya ya sauke ya sake duban wayarsa dake haskawa Bai daga ba kawai ya tayar da motar ya juya ya nufi gidansu, dan ba zai je wajen abokanan nasa ba, haka kawai yake ji idan ya je yana iya sauke fushin da ba nasu ba a kansu Mikewa malam Barau ya yi yana lekawa kafin ua juyo yana kama haba ya gyada kai ya ce" Ikon Allah, ni ban taba gannin gida irin na bawan Allahn cen ba, ka ga fa malan Saidu sai ya je ya dawo daga kasuwa da ledoji na kayan kwalam da makulashe ya shige ciki ya sake tirke kartin yan matan cen ya ciyar ya yi barci harda minshari safiya na yi ka ganshi kalau abinsa....., To ni Allah na tuba ko daya na girke irin ya'yansa ai ba ni ba rintsa ido kalau kamar wanda bani da damuwa a duniya, ba zan taba iya rintsa idannuwana ba dan ya'ya mata ai fitina ne, ka ga du sun kamo shi a tsayi biyu jikaka biyu mudil mudil ama baya ko yar suman nan ta badi? A gaban idannuwansa a shiga a fita ana rawar nanaye wai yan mata ne? Ka ga yanzun itama wace ake cewa bakin aljani ne ya sa bata da mashinshina ta fara shiga motocin karti!" Malan Agali ya zubo shayi ya juyo yama miko masa ya ce" Kai wani bakin aljani, malan ai wannan y'a ta Malan Saidu garke ce ciyar da ita sai makiyayi, sau nawa ana kwatanta tunkararta sai ace tsoronta ake ji?, Wannan y'a da ka gani ina fatan gannin namijin da zai dauka, kuma motar cen da kake gani inaga ta wannan elhajin ce da yake shiga gidan nasu, ni na rasa a ina suka samo shi, mutun mai kudi yana shiga gidan motar cen tasa ce ni na santa" Na Awa ya fyace abin raken dake bakinsa ya fuskanci Barau da Agali ya ce" Ni ka ga da za'a bani y'ar nan, tsaf zan aura, Allah na tuba Malan Saiduma ya iya da mace irinta bale ni? Kai dai abu daya nake tsoro da shi da ka ganshi a nan lange lange sai masifar karfi, bana son na shiga lamrinsa ya kwasheni ya watsar a anguwa da yan jikoki da sirikai fita ta gagareni, dan tsaf tasalah zata ajiye min dandali a bayan layi ta tsigeni , ita har yanzu bata hakura da ni ba ni kuwa na gama aure da kazama, tasalah fa ko jini ta gama bata wankan kirki sai shafe wai yawan zubawa fata ruwa na raurautar da ita, ji fa masifa?......." Hakane, wannan zamani ya zo mana da abin mamaki, maza sun dauri aniyar yiwa mata shiga hanci da kudundune harta dan tsegumin da ake kira na mata nema suke su mana fin karfi, kiri kiri yanzun idan namiji ya dara biyu basa jajen nema da turbisa sai su aro kalabi su yafa su nemi yin shige cikin shingen nazaru.....zamani kennan babu ruwanka da wani ama kana fama da tunaninsa.... Allah shi kyauta TAUFEEK direct gidansu ya nufa, Baban gidan fitacen dan kasuwa nagartacen mutun mai kyauta da kari, mutun mai sadaka da tausayin talakawa, wanda aka fi yiwa lakabi da *MAI KWANONI* Kasancewar get din a bude sakamakon bakin da aka yi daga cikin gari na mahaifinsa ya sa ya bi bayan motocinsu kafin ya yi baya ya ganganra cen gefen da ake ajiye motocin gidan ya dakatar da motar a hankali ya kashe ya sake duban wayarsa da yanzunma ake kiransa kiran kuwa ya tabata idan har ya yarda ya shige bangarensa ba tare da ya daga ba yanzu zai ga wace ta isa da shi ta tardo shi ta kuma wanke shi soso da sabulu, a dole ya juya baya ya dauko ledar kilishinta da kuma embulop ta maganinta da ya siyo sannan ya rufe motar bai ko dauki wayar ta wajen KAUSAR da ta dawo masa da abinsa ba A nutse ya nufi bangaren Matan gidan, watau matan Elhaji 💔💔💔💔❤‍🩹❤‍🩹💔💔💔💔 *DA CIWO A ZUCIYATA* 💔💔💔💔❤‍🩹❤‍🩹💔💔💔💔 _MALLAKIN_ *SAJIDA NIJAR* *FREE BOOK NE* 4️⃣ LITATAFAN MARUBUCIYAR Duk karyar kada Yar mahaukaciya Neman na kaina Bani da zabi Bak'a ce Kutkale Makauniya ce Mage Duk nisan jifa Idan ka raina inda kake Dutse Alkalamin kadarata Bani da zabi Dakika Biyar Now *Da CIWO A ZUCIYATA* *Tallah, tallah, tallah* *SECRET DE LA FEMME DU MANGA* _Gidan Kamshi, Sirrin Manyan Mata, nesa tazo kusa,Amarya ,Uwar gida,Ango da mai gida Har ma da yan mata da samari shin kuna sane da cewa HAJIYA FUSAM ta shirya tsaf domin gwangwaje ku da turarakunta masu dankaran kamshi? Tare Kayan gyaram jiki na musamman ,wanda daga nesa kamshin ki kadai ya wadatar ya isar da sakon zuwanki waje,gidan ki kuwa sai ya zam abun kwatance wajen kamshi, kar na cika ku da surutu bara in fara zayyano su_ Farar Humura Bakar Humura Humura special, humura de bain Humura epicé Lait de nuit Parfums désodorisant Parfums rideau et dras Lait de nuit Alkam Kulakcam *Waɗannan kadan ne daga bangaren turaran ruwa* Gagab, sandal flex, Durot, durus, sandal fleur, tafarce, farce, sandal bangui, sandal, hypotonic sandal, al'ut, coktail creation VIP, Gajiji, Mankaji, turaran wutar labule da cafet, Aba malan, boulettes *Munada bangaren gyaran jiki kamar haka:* mai mai saka santsin jiki, mai mai kanshi, Kayan gyaran jiki mai saka fata ta yi santsi da laushi, kayan gyaran jiki mai saka fata ta yi fari, Sabulu mai saka fata ta yi haske, sabulu mai saka fata ta yi santsi, sabulu mai goge yanayin fata, mai wanda baya saka fari mai gyara fata Sayen na gari mai da kudi gida,sai an gwada akan san na kwarai💃💃 Hajiya Fusam na zaune a kasar Niger domin yin magana da ita kai tsaye tuntuɓi wannan number 97 82 44 94 *SECRET DE LA FEMME DU MANGA* Gidan Kamshi, Sirrin Manyan Mata💃💃💃💃💃 A nutse ya nufi bangaren Matan gidan, watau matan Elhaji yana sauke idannuwansa a kan kannensa uku dake zaune a baban filin kofar dakin mai dauke da farin tiles da shukokin da duka zagaye wajen sunna bitar karatun islamiya, ya tabata malaminsu bai jima fa tafia ba ya kuma basu assignment na yi Amsa gaisuwarsu ya yi da kula, sai kuma ya dakata dan a lokacin ne kanwarsa mai sunna ISHRAT ta taso da ladabi ta ce" Yayanmu, Aba yace idan ka shigo ko wani lokaci ne ka je baya samunka a wayarka" Jim ya sake yi a dole yana dan kallonta kamar itace ta kar zomon, dan maganar sai ta so dauke masa a harshensa domin ya so ne yace da ita Aban na nan? Sai ya ji ya kasa ciro kalmar a dole ya juya kawai ya shige tankamemen falon gidan nasu mai dauke da bangare bangare na falo uku dauke da kujeru saiti uku kala daban daban da kwaliya irin ta manyan mata masu maiko a baki Takalminsa ya cire , sai farar safar kafarsa ya idasa shiga Matan mahaifinsa su biyu dake zaune a falon Hajia FATAHEEYA sunna hira ya karasa da kula sosai da kuma ladabi ya gaisar da su kafin ya mike ya shiga haurawa sama bayan sun gama gaisawar dan nufa bangaren mahaifiyarsa hankali kwonce ya bacewa ganninsu Shiru ne ya ratsa wajen nasu bayan tafiyar tasa, shirun har na dan lokaci domin kowace shirun da ta yi a cikin zuciyarta tana tunanin abinda ya tsaye mata a rai ne wanda yake damuwarta ko jin dadinta, sai dai a irin yannayin fuskarsu ba sai an tambaya ba abin tsaye masu ne ya yi , ba damar amayarwa, dan ko a tsakaninsu babu wace ta yarda da y'ar uwarta, zama ne ake yi na bugun ciki da munafurci, kowace na boye kalar wasanta ne dan sun yi wayon da ba zasu hada kai da kishiya ba, komai dadin dan miji ai ba d'ana bane...in ji Hajia NUWAIRAH Wannan d'an daya cilo namiji ya zame masu wani baban gibi mai wuyar fasara Shi din nan shine baban damuwar cikin kuryar zuciyarsu Idan suka yi tsai suka duba irin girma da darajar da yake da ita aa cikin gari kadai sai su ji inama ace da wani gagarumin ciwo suke fama da wannan faduwar gaban Irin daukakar da yake da ita a aikinsa, wanda yake matsayin baban likita aka nuna masu kuma ua dawo karatu,karatun wani munafurci? Kuma mahaifinsa ya ja maganar idan suka fitar da sirrin yaronsa daidai suke da fita a gidansa ya sake hadasa masu wutar kiyaya boyayiwa fiye da ta kishi Juyowa Hajia NUWAIRAH ta yi bayan ta saisaita yannayin fuskarta sukai ido hudu da hajia FATAHIYA Murmushin yake da ya fi kuka ciwo suka sakarwa junna , cike da isa irin ta isasun mata Hajia NUWAIRAH ta ce" Muna da shagali baba a gidan nan idan auren Elhaji karami ya tashi" Da dan yanga da basarwa Hajia FATAHIYA ta dan yarfe hannu da cikinta a gaba wanda duka duka watansa biyu a jikinta ama idan tashi zata yi tana turo shi in zama haka dan abin nema ne ya samu ta ce" Ai kam, na san ranar ke uwar ango har kya yi kari da zinari dan farin ciki, Allah ya nuna mana" Murmushin ta yi itama , ama bata bada amsar Adu'ar ba, karshema sai ta mike tana nufar sama bangarenta dan abinda ke ranta lalle lalle sai ta amayeshi zata ji dadi Tana bude dakin nata ta ga yarinyar wajen yayanta da take riko wace tun tana karama aka bata zaune tana waya a saman kujera Direct ta karasa inda take ta karbi wayar gana duba da wanda suke wayar, gannin sunnan kawarta ya sa ta mika mata wayar sannan ta nufi bayi tana ta dane abinda yake tukarta, dan kuwa ba kowa ne ya san me take ciki da asalin d'an mijin nata ba Tana shiga ta rufe ta karasa ta kunna ruwa sannan ta cire dan kwalin kanta ta kama kanta da hannayenta bibiyu dake sara mata Ta jima a haka sannan ta dago kanta idannuwanta na sake yin ja ta kalli madubin da idannuwanta da suka yi kamar sun rine na bacin rai sannan ta girgiza kanta tana sakin murmushi mai ciwo ta ce" Na tsaneka kamar yadda na tsani mutuwata!, Lalle zan rayu da burin gannin bayanka! Ba mutuwarka nake so ba, ka tagayara ka zamo dan daudu, ka zamo wanda ana takamar kaine namiji daya jal da aka haifa ama kuma ba anfani, yadfa uwarka ke rayuwa da farin cikin kai daya jal ta malaka tana ji tana gani zaka salwanta ka daura zani elhaji ya tsine maka ya kore ka! Yadda ubanka ya sakar maka ragamar dukiyarsa na rantse da wanda raina ke hannunsa sai ya kuleka saboda dukiya domin sai na yi sanadiyar da zaka zamo tamkar kare a bin mata, mai kuma shaye shaye dan kuwa du wanda ya auri bin mace ba zai taba ajiye dukiya mai albarka ba komai kudinsa, a haka zaka karar da dukiyar ta yadda sai ya yi shara'a da kai sannan ya tsine maka ya koreka!, Wannan alkawarina ne!"............. Da kyar ta iya saisaita kanta sannan ta fito muryarta bata fita da kyau ta ce" Ke Hamdiya Ajiye wayar nan maza ki sauka ki ce da auntynku na shiga nafila ba zan sauko ba dan kar ta ga shiru" Ajiye wayar Hamdiya ta yi ta dauki hijab dinta ta saka sannan ta fice, dan kuwa dokar gidan ce, ko mace dokar yayansu ne ya masu hani yawo ba hijab ko shigar da zata rufe suturarsu sosai koda a falo ne, idan dai so kake yi ka yi yawonka tsirara ko da shiga ta rashin da'a cen ka kule dakinka ka yi, in kuwa ka yarda ka fito da shigar da ba ita ba aka yi rashin dace ka hade da shi a ranar tsag zai darwaye maka fata kuma babu abinda za'a yi Da takaici ta kule ganninta a kan Hamdiya ta karasa saman kujerar cikin dakinta na farko ta zauna tana kada kafa........., Watau du iskancin FATAHIYA baya gabanta, wani jiji da kai a kan ciki ko? Ba shine a gabanta ba, abinda yake gabanta wannan ne, ta tabata ko yan biyar maza Fatahiya zata haifa ta riga ta makaro tunda kafin su zama abin alfahari ta gama jigatuwa, ama wannan basamuden mai balagagiyar iskanci da tsiron rashin kunya ko? Ya gama yi mata kaka gida da ya'yan gidan baki daya, ita saima ISHRAT ta shigo ta ci ubanta yau, yarinya sai kunnen kashi, irin yadda take yiwa ƴaƴansu biyaya na ci mata tuwo a kwarya, zata daidaitata ne , dan ba zai tana yiwuwa ta zama aminiya a wajen makiyinta ba! Murmurshi ne kwonce a saman fuskarta tunda ta buda ledar kilishin nan ta gani Kanta ta dago dan yi masa godiyar dawainiyarsa a kanta, domin koda ta zamto mahaifiya a gareshi baya hannata yi masa godiya a duk lokacin da ya kyautata mata, sai ta ga a tsaye yake a wajen da ya mike tun bayan gaisheta da ya yi ya ajiye ya mike Sake tsura masa ido ta yi kafin ta dauke kanta ta ce" Kai zauna mana " Inda ta nuna masa ya kalla, sai kuma ya zauna yana sada kansa Baki ta tabe ta ce" Ka leka Hajia ne?" Kai ya girgiza dan rabonsa da kakar tasa tunda sasafe da ta kai masa maganin baki da na basir ta saka ya sha ta kuma tofe shi da yawu ciki da bai Baki ta kuma tabewa ta rufe ledarta da kyau ta ajiye a gefe ta ce" Baka da lafia ne?" Kai ya dago wannan karron ya dan kalli mahaifiyar tasa, sai ya kuma gimtsewa yana ayana yanzu zaka amshi sakamakonka a hannu TAUFEEK tunfa baka tausayin kanka Mamansa ta tabe baki tana harararsa sama da kasa kafin ta dauke kai ta ce" Kai dilla tashi ka bani waje, bana son shashanci kuma ni ba sa'arka bace da zaka zo har dakina ka min rashin kunya!, Kai in banda iya shege ni zan ringa magana kana yarfawa? Ka kula ni ba Hajia bace kuma ni ba elhaji bace tsaf zan wanke fuskar yaro da mari, tunda dai lafiyarka kalau sarautar da baka gada bace ta motsa sai ka yi, daga nan ka je wajen ubanka yana nemanka kuma ka je wajen HAJIA ka san in bata ganka ba yanzu zata hauro nan ta bi daki daki ta barmu da Allah, ni ka rabani da rikicin da ya fi karfina ka ji na fada maka! Jeka kawai jeka walahi tun muna mu biyu!" Murmushi ne ya subuce masa a hankali ya sake dago dubbansa yana kallon mamansa, watau ba zai tana yin tsufa da a dura masa ba dadi ba a gaban mahaifiyarsa.........har ga Allah sai ya ji wani sanyi sanyi da farin ciki, hakan ya sa ya dan sake kureta fa kallo ta fitar da kilishinta ta fara ci ya ce" Yanzu Mama dama sarauta ta fi kudi ne?, Ai asalim mulkin kudi ne Hajiar Babanmu" Dan kwalinta ta turo gaba ta nemi ajiye ledarta, Yana gannin hakan ya mike da dauri ya fice yana sakin murmushi harda rike hularsa dake son faduwa dan fitowar da ya yi ta dan makalu da kofa Dakatawa ta yi itama tana yar dariya kafin ta girgiza kai ta karasa wajen wayarta ta daga ta amsa mijinta fa fadin eh ya shigo gayanan zuwa bangaren nasa Wayar ta kife a hankali tana lumshe idannuwanta hadi da ambaton sunnan Allah...., Sai kuma ta yi shiru a zuciyarta ta shiga yi masa addu'a, duka kaf aduo'in da ta saba ta yi masa kafin ta mike ta karasa kusa da kilishinta, ta janyo ta zauna tana murmushi ta shiga ci A bangaren mahaifinsama zama suka yi da bakin nan harda shi suka dan sake zantawa kan abinda ya shafi ci gana na harkar kasuwanci sannan bakin suka yi masu salama mahaifinsa ya masu rakiya shi kuwa ya zauna yana dan shan tea din da aka dafawa abansa Dawowa MAI KWANONI ya yi yana murmushi ya zauna yana ta amsa wayar abokinsa Yana gamawa ya maida hankali kan Ɗan nasa ya ce" Elhaji karami yau ina aka wuni ne?, Tun safe rabona da kai" Yar dariya ya yi yana shafa gaban goshinsa ya ce" Aba ka manta da maganar dilolin gwonjon da suka sauka yau? , Sai dazu na gama daga cen kuma na leka wajen KAUSAR" Murmushi mahaifin nasa ya yi yana rage amon TV dake watso labarai.......... Da kula ya ce" Masha Allah, an yi zumunci kennan, fatan du sunna lafiya" Shima da kula sosai da ladabi ya amsa mahaifinsa sai kuma shiru ya dan ratsa Shi mahaifin nasa tunanin da yake yi shine har yanzu da ace za'a bi ta tasa da ya kawo maganar wannan zumunci na yaronsa da KAUSAR, sai dai zamani ya zo da salo kala daban daban, shi din kansa ya yarda cewa kawance ne kawai dan kuwa an yi abubuwa kala kala da da ace ba kawancen bane da ya gane , sai abin ya nuna kawancen ne kawai A hankali ya ce" Damgane da maganar YUMNAH, bana so maganar ta wuce bayan sallar nan, mun tsayar da mahaifinta bayan sallah da sati daya kawai a yi, yaya ka gani?" TAUFEEK ya sake sada kansa kasa sosai...., Yumnah dai na daya daga cikin yan matan da ya tsaya ya karanta har ya ga eh ta cencenci zamowa iyali a wajensa, domin ta fito daga gidan datijai na kwarai haka kuma tana da tarbiya, uwa uba idan ya yi magana ko wace iri ce YUMNAH na yi masa biyaya domin tun daga lokacin da ya kai mata hijabai yace daga yau su yake da bukatar ta saka ta amsa take kuma sakawar......zai iya cewa eh yana iya auren YUMNAH harma ya rayu da ita a matsayin matarsa idan har alkhairi ce ita din a rayuwarsa......, Sai dai ya so ace bayan an gama exam dinsu an jima sosai ne, dan kuwa bayan sallah da sati daya koda an fitar da result din ba zai fi da kwana goma ba, ga ginnin clinik da yake kai, abin kamar zai dan cakule masa ne ko menene Dan murmushi mahaifinsa ya yi, sada kan yaron nasa ya saka shi jin dadin hakan, TAUFEEK bai taba barin nagartatun halaya ba, shi yasa bashi da darr da yaron nasa, bashi da wani darrr a kan lamarin TAUFEEK Abansa ya dora da fadin" ka yi magana hakan ya yi ko yaya?" Dan murmurshi kawai ya yi a hankali ya gyada kansa Mai KWANONI ya ce" Masha Allah, sai kuma maganar umarar Hajia, ka ga na so ta yi hakuri su tafi da su ISHRAT, ama ta kiya, bafa zata je da kowa ba sai da wanda ta saba zuwa, na dan so kwatanta mata abubuwa kamar zasu maka yawa ama firr Hajia ta ki Maganar dan da na nuna mata kana Dubai idan ka dawo ka gaji sai cewa ta yi to shikenan a bari badi idan ranta ya kai sai ku je" Baki ya dan tabe yana ayana irin cazar tsohuwar cen da zai yi, ita me yasa ba zata barshi ya dan ji da abubuwan dake gabansa bane? A gidan nan bai isa ya yi barcin safe ba yanzu zata zo ta ringa taba masa wuya tana faman fadin bashi da lafiya ina manemi da barcin safe?, Idan ya ki yi mata abu sai ta hada shi da wace ta isa da shi ta koma gefe abinta, HAJIA sai ya yi maganinta saboda maganar zuwa umurar nan, zata yi bayani ne Ama sai ya ce da mahaifinsa" Ba komai Aba, in sha Allah zamu tafi harda su Ishart dinma" Murmushi mahaifinsa ya yi ya ringa saka masa albarka, shi dai idan har TAUFEEK na duniya baya tunanin zai hadu da damuwa ko ta mecece, idan ta shigo kuwa da yardar Allah TAUFEEK zai gushe masa ita ko ta wanene, shi yasa a duniya bayan mahaifiyarsa baya hada soyayar yaron nan da kowa, kuma baya jin akoy abinda zai iya malaka ya masa shamaki da shi a nan gidan duniya, babu shi Dan hira suka taba sannan ya mike ya karasa bangarenta yana jin gajiya sosai Dan dage labule ya yi , ai kuwa karaf suka yi ido hudu da ita tana faman auka turaran wuta na jiji a wani makeke kasko dauke da rabshi tari guda Murmushi ta saki hadi da fan bangalar da dariya tana dan matse ido dan ta ganshi da kyau ta ce" Shigo mana magidanci zo ka sha kanshi, ka san shi turaren jiji bayan kanshi da dadi kuma maganin mayu ne da aljanu" Harara ya sakar mata yana jin zai kware, dan har ga Allah turaren nata kauri ne yake yi na tashin hankali ama sai faman fadi take wai kanshi, wai wani maganin aljanu, ai itace aljanar ba kowa ba! Sakin labulen ya yi ya yi tafiyarsa hakan ya sa ta sake zuba idannuwanta tana kallon kofar kafin ta kallo Hamdiya da ta yi kamar ta suma zuciyarta na bugawa tana kallon hanyar da ya yi tafiyarsa yau ko shigowa ya dan zaunan bai yi ba bale har ta kare masa kallo ta ce" Ke Hamatu yaron nan ya tafi hala?" Hamdiya ta dan sauke ajiyar zuciya ta ce" 💔💔💔💔❤‍🩹❤‍🩹💔💔💔💔 *DA CIWO A ZUCIYATA* 💔💔💔💔❤‍🩹❤‍🩹💔💔💔💔 _MALLAKIN_ *SAJIDA NIJAR* *FREE BOOK NE* 5️⃣ LITATAFAN MARUBUCIYAR Duk karyar kada Yar mahaukaciya Neman na kaina Bani da zabi Bak'a ce Kutkale Makauniya ce Mage Duk nisan jifa Idan ka raina inda kake Dutse Alkalamin kadarata Bani da zabi Dakika Biyar Now *Da CIWO A ZUCIYATA* *Tallah, tallah, tallah* *SECRET DE LA FEMME DU MANGA* _Gidan Kamshi, Sirrin Manyan Mata, nesa tazo kusa,Amarya ,Uwar gida,Ango da mai gida Har ma da yan mata da samari shin kuna sane da cewa HAJIYA FUSAM ta shirya tsaf domin gwangwaje ku da turarakunta masu dankaran kamshi? Tare Kayan gyaram jiki na musamman ,wanda daga nesa kamshin ki kadai ya wadatar ya isar da sakon zuwanki waje,gidan ki kuwa sai ya zam abun kwatance wajen kamshi, kar na cika ku da surutu bara in fara zayyano su_ Farar Humura Bakar Humura Humura special, humura de bain Humura epicé Lait de nuit Parfums désodorisant Parfums rideau et dras Lait de nuit Alkam Kulakcam *Waɗannan kadan ne daga bangaren turaran ruwa* Gagab, sandal flex, Durot, durus, sandal fleur, tafarce, farce, sandal bangui, sandal, hypotonic sandal, al'ut, coktail creation VIP, Gajiji, Mankaji, turaran wutar labule da cafet, Aba malan, boulettes *Munada bangaren gyaran jiki kamar haka:* mai mai saka santsin jiki, mai mai kanshi, Kayan gyaran jiki mai saka fata ta yi santsi da laushi, kayan gyaran jiki mai saka fata ta yi fari, Sabulu mai saka fata ta yi haske, sabulu mai saka fata ta yi santsi, sabulu mai goge yanayin fata, mai wanda baya saka fari mai gyara fata Sayen na gari mai da kudi gida,sai an gwada akan san na kwarai💃💃 Hajiya Fusam na zaune a kasar Niger domin yin magana da ita kai tsaye tuntuɓi wannan number 97 82 44 94 *SECRET DE LA FEMME DU MANGA* Gidan Kamshi, Sirrin Manyan Mata💃💃💃💃💃 Hamdiya ta hadiye yawu da kyar tana sauke ajiyar zuciya ta ce" Eh HAJIA ya tafi" Hajia ta shiga kiciniyar tashi tana fadin" Kai, to me yake damunsa? Nifa bana son na ga magidanci a haka, yaro yana tafe ana harararsa kar aje an shiga gaban jikana ina nan zaune, ke Hamata bani lawurjena na bi bayansa, cikin jakata kuma akoy dan damaso hado min da shi da kulin kaka ka yi ka fito na je na turara masa, aniyar kowa ta bi shi in sha Allahu yaron nan sai ya zama shugaban kasa sai dai maki gani ya mutu!" Mikewar ta yi domin idan har bata yi gagawa ba HAJIA na iya wanka mata mari, a kan lamarin Yayansu bata ji bsta gani, harta mahaifiyarsa na kiyayewa dan kuwa a kan TAUFEEK ko Aba sai ta batawa bale su Yana kokarin zama a luntsumemiyar kujerar falonsa, wayarsa a kunnensa dan kiran da YUMNAH ke yi idan bai daga ba har ta yi kuka ya santa sarai ya kai dubansa wajen hanyar shigowa dan jin motsi Abubakar ne ya shiga shigo masa da kayan abinci Kansa ya dauke daga dubansa a hankali ya ce" Sorry YUMNAH ba zan samu zuwa ba yau na gaji" Har ga Allah sai da ta ji wani irin hawaye na neman tsinke mata, da wani irin daci a cen kasan zuciyarta na tunanin abu dayan biyu Itafa idan har ba gani ta yi an daura aurenta da TAUFEEK ba da wahala hankalinta ya kwonta da wannan KAUSAR din Ita ta rasa a wani bigiri zata ajiye wannan shirmen, kana zaune kalau da mutumen da ake kira miji a gareka nan da kwana kusa ama kiri kiri kana fuskantar kusanci da shi da wata macen cen da yake kira da kawarsa fiye da kai? Sau biyu sunna samun matsalar da TAUFEEK ya dauke mata kafa kwata kwata na tsayin lokaci, ta ringa bibiyarsa itace nan , itace cen ya ki sauraronta, har gidansu ta zo fir ya ki kulata, tana samun KAUSAR ta mata bayani ta mata fadan itama laifinta ne ta daina kula kowa tunda bata so ta kuma mata alkawarin ya wuce a washe gari TAUFEEK din ya amsa kiranta?, Bayanshi kayan sallah wannan idan za'a yi mata ta sha gannin an mata wani abun iri daya da KAUSAR bayan wannan kyauta ce ta mahaifiyarsa bama tasa ba, abubuwa ire iren haka idan har irgawa zata yi sunna da yawan gaske, sai gashi yauma an maimaita abinda aka saba yi mata sai ance mata za'a zo a fasa dan an je an zauna a wajen KAUSAR an cika dare ana hira, itafa zata iya rantsewa da Allah ko yan matan da suke amsa matsayin yan matansa a gari basa yi mata katutu a wuya irin na wannan baiwar Allahn, sam bata da nutsuwa da ita, bata son lamarinta, ama ba komai in sha Allah lokaci dai idan har ta amsa sunnan matarsa kuma zata maida hankali ta fara haihuwa du taurin kaan TAUFEEK ai dole zai daina mu'amalantar mace a matsayin kawa ko dan tarbiyar ya'yansa.....ita abinda ya fi bata mamaki mahaifinsa fa ya san da maganar KAUSAR ama bai hanna ba, ba'a maganar mahaifiyarsa dan ta kula sonsa take sosai , ama ba komai a juri zuwa rafi wata rana tulun zai fashe ne! Hajia yake kallo da kaskon hannunta hakan ya sa bai gane jimawar da YUMNAH ta yi bata yi magana ba har sai da Hajiar ta saki murmushi tana sakace hakorinta da tsinke ta ce" Kun gama maganar ne?" Idannuwansa ya lumshe a hankali ya ce" YUMNAH?" YUMNAH ta ja hanci tana share hawayenta kasa kasa sosai ta amsa TAUFEEK ya ce" Kuka kike yi ne?" YUMNAH ta ta fashe da kukan da ta kasa hanna kanta tana sauraronshi, hakan ya sa ya dan sake lumshe idannuwannsa da suka dauki launin ja a hankali ya ce" Zan fa zo gobe in sha Allah, menene na kukan kuma?" YUMNAH ta ringa jan hanci tana hanna kantaa kukan, a hankali ta ce" ka tabata gobemaa ba zaka tafiyarka wajen KAUSAR ba?" KAUSAR........sunnan da ta ambata ya saka shi jin wani takaicin da ya dan barshi ya sake kule masa wuya Yanzu KAUSAR ba zata taba girma ta yi hankali ba Fisabililahi? Inama abinda ya yi mata, bata tsaya ta ji aiken Aba bane, bata tsaya ta ji bama ya kasar Dubai ya tafi shigowarsa jiya , yau yana fama ya gama da wasu kayan ya je ya sameta ama shine ta watsa shi? Shi KAUSAR ke hanna Auta gaisarwa? Shi KAUSAR ke cema in ta haihu yar halak ba ita ba maganar ya gyara kayansa? Wai shi ya gama menema tace? Itace mene? Lalle KAUSAR ta kirta masa rashin hankali wanda ba zai taba mantawa ba, kuma shi da ita su zuna za'a ga maganar da ta yi wa zata komewa, ba tace in ta kuma masa maganar ya yi karatu ba meye meye? Zai ki yin karatun za'a gani waye zai cika dare yana fadim ya yi karatu, ita in bama ta raina shi ba shi sa'anta ne zata wanke shi soso da sabulu kamar wani danta?, Har ga Allah a gari kaf ya zagaya da kwakwaluwarsa bai ga dan jagaliyan da zai yi wannan gagancin ba bale mai hankali, kama daga kan mace har namiji sai KAUSAR, shi shi???? "Ana halo halo a wayar magidanci amsa mana ka gama na ji kukan uban me take yi ita kuma? Ba dai gaba take saka ka tana maka kukan rainin hankali ba salon a raba maka hankali biyu, jigilar gidan nan ka yi ko rikicin munafurci na mata? Ni fa ka ga du macen da za'a aura maka sai na kaita kotu ta yi rantsuwar ba zata cuta maka ba dan bana son rikita rikitar yan matan zamani yan iska masu taba halitar ALLAH sunna zanna gira da kwaliyar aljannu wai su masu kyau" ta karashe tana sake gyara tsayuwa ta dauke kai daga kallon da yake yi mata kamar ya ga bakuwar halita harda zarro ido yana kallonta da mamaki Dididif din wayar ya saka shi kallon alon wayar sannan ya sake kallon Hajia dake harare harare Kasa kasa kamar kar wani ya ji shi ya ce" Kin kuwa san wacece kika zazage tas ?" Hajia ta juyo tana maka masa harara ta ajiye kaskon ta watsa magungunnan da ta harhada ta yi raf da hannunsa da ya kawo zai kautar da hayakin da ya shiga binsa bududu tana gyatsine ta ce" Ko wacece uwata, nace uwata in itace mai KWANONI kuwa ni nice babarta!, Alkur'ani idan baka san ciwon kanka ba na san ciwonka babu wace zata lalata maka zaman lafiya ta maka kukan kirsa ta cuceka ina raye!" Har ga Allah bashi da karfin rikicin yau, haka kawai yake jin karfinsa ba na rikici bane yau, ga hayakin nan juya masa kai yake kamar zai sume bayan tace na mayu ne da na aljannu, shi kuwa ba maye bane a sanninsa haka kuma shi ba aljani ba, hayakin ne kawai bai cika so ba har wani makaki yake masa a wuya, ama ta ki ganewa sai da ta gama rikita masa rayuwa ta saki tana jan tsaki ta dauka ta ringa zagaye kujerar da yake zaune tana tofe shi sannan ta yi gaba tana ta fadace fadacenta Idannuwansa a lumshe suke ya zuba su a kan hanyar da ta bacewa ganninsa a kala ya dauki minti biyar kafin ya sauke ajiyar zuciya ya shiga bude abincin ya shiga ci dan yinwar dake cikinsa idan ya kwonta ga takaicin Kausar, ga na Yumnah, ga na Hajia ana iya tardoshi ya karkace da hawan jinni, gwara ya cencani kansa tunda rayuwar ta zama haka Sun dan jima kafin suke shigowa kusan a tare a lokacin Aba tuni ya dawo gida ya ci abinci ya shiga karatun Alkur'ani domin shi wannan lokacin kadai yake da shi wanda yake yin ibada sosai, dan kuwa idan ya fita nema baya zama sai dare ya yi kafin yake samun zama Bayan sun huta Aban ne ya saka aka masa kiransu su dukansu ukun, Sun jinginu ne a jikin garu kwon fitilar da nepa sula kawo ya haske dakin, hakan ya sa yake binsu da kallo daya bayan daya harda Mamansu Auta kuwa yana cen saman katifa yana barci abinsa Numfashi ya sake saukewa zuciyarsa a tsintsinke ya shiga bayanin abinda ya wuni da shi a saman zuciyarsa wanda bai shigo gidan nan da wuri bane saboda sai da ya je wajen manyansa ya duka ya nemi shawara kuma aka amince masa da hakan harma aka sake bashi shawarwarin da zai ji dadinsu A tausashe sosai ya ce" KAUSAR, A'isha, RUKAYA, na tara ku a nan ne dan na ji daga bakinku dangane da maganar aure......." A cikinsu su biyun nan wani irin salama ne ya sauka a kahon zukatansu, ita kuwa wani irin firgici da tashin hankali ne ya dirar mata bayan fushin fadanta da yaron cen da ya raina mata hankali Kanta a kasa yake, ama mahaifinta yana iya gane halin da take ciki domin ta kama hannunta sai murzar yar yatsarta take yi haka kuma kaffafuwanta dake hade daya kan daya sai murzasu take yi tamkar tana jin fitsari ya matsotan nan Idannuwansa ya dauke cike da rauni ya sauke kan fuskar matarsa Irin kallon da take masa mai dauke da girmamawa da mutuntawa da nuna alamu na tana tare da shi ya saka shi jin dan kwarin gwuiwa a hankali ya ce" In sha Allah gobe da safe ina jiran amsarku, kowace ta yi kokarin gannin ta bani amsar da ta dace mai kyau wace zan yi bincike a kai dan mu samu matsaya daya mai kyau, domin bi'izinillah shekarar nan idan har ta wuce ku babu aure to zan samo maku Wa'inda suka dace na hadaku na aurar, ku tashi maza a je a kwonta a huta, du wace bata yi shafa'i da wuturi ba ta tabatar ta yi kafin ta kwonta" Amsawa suka yi su biyun, ita kuwa kai kawai ta iya gyadawa tana jin hankalinta na karra tashi A hankali ta mike dan bin bayan yan uwanta , mahaifinta ya yi kiran sunnanta yana dauke dubansa daga kan mamanta dake masa alamun kar fa ya nuna gazawarsa Juyawa ya yi ya ciro yar karamar wayarta da ta bashi ajiya tunda zasu fara jarabawa ya miko mata yana dan murmushi ya ce" Dama ga wayarki nan ai na san za'a samu kira yau ko?" Wayar ta kalla, sannan ta kalli mahaifinta..... Za'a samu kira?, To daga wajen wa? Sai dai bata da amsa, hakan ya sa ta yi godiya ta juya ta fice ta karasa dakin itama ta kwonta saman katifarsu ta juya tana fuskantar garu Tun tana jin maganar yan uwanta sama sama sunna waya da albishir wa masoyansu cewa Abansu ya yi tambaya kan abinda ya shafi zumuntarsu da sake jadadawa zumuncinsu da karra yarda in har alkarsu da burinsu na nan? har shiru ya wanzu a dakin a hankali minsharin Rukaya ya fara tashi hakan ya tabatar mata cewa sun yi barci ne Idannuwanta kekyashe suke ba alamun zasu risina ko su aro barawon da aka sheda kwarewarsa a sata dan ya saceta ko dan wuni da ta yi a kai kawo da jigila kala kala na auren da aka yi yau, ama shi sarkin baiwa bawa kunya shiru bai dauketa ba, bai yi alamun zai dauketa ba A hankali ta dago hannunta da ya sage ta dafa ta mike zaune sannan ta jinginar da bayanta a jikin garun ta kurawa waje daya ido Wani irin hawaye ne mai dumi ya shiga kokarin saukowa daga cikin kurmin idannuwanta dan zubowa saman fuskarta a lokacin da ta shiga tambayar kanta shin menene laifinta ? Menene laifi dan ta zamto mai rufe jikinta?, Menene laifi dan Allah ya haliceta a yadda ya haliceta? Ita dai ba mai munin da za'a ce kai wance kuwa akoy muni ba, dan har fadi ake yi ta fi yan uwanta dorinar kyau kawai dan bata fitar da kyan ne......, Sha nawa ake cewa da ace zata yi kyale kyale irin na yan mata ta yada wannan hijabin da ta ga maza na biniyarta kamar kuda, mutun nawa suka ce idannuwanta, girarta, karan hancinta, bakinta abin kyau ne a idon mai kallo koda kuwa baya so.............., Fatar jikinta mai haske ce domin ta yi hasken mahaifiyarta ne, yannayin jikinta ba dati ba wari, shin wannan bai isa namiji nagartace ya nuna yana yinta ba?....., A yanzu dududu idan ta ajiye rayuwar nata a fili ta duba ba zata ce ga tsayaye nan da ya nuna mata aure yake so ba, ita fa kunyar yin zancema take ji, haka kuma kunyar yin saurayinma take ji, ita baban abinda ya fi bata kunya ace za'a mata aure itama, duda ta dade da yarda cewa auren nan ka so shi ko ka ki shi akoy lokacin da jiki ke amsawa hankali ya damu da bukatar abokin halita sai dai idan ka ki bada hankali ka yi watsi da lamarin a samu sasauci ba wai a daina jin bukata irin ta hannun bawa a jikin baiwa ba! A yanzu shekara ashirin da shida kennan tana rayuwa, tunda ta yi ashirin da uku ta ga haila, a hankali ta shiga saka rigar mama duda ba wadatatun maman ne da ita ba ama mamansu bata yarda dan baiwa Maman kariya da zubewa ko lalacewa, ....sannu a hankali take fuskantar kaikayi irin na jiki mai zuwa ba dole sai an gayato shi ba, a hankali ta koyi korarshi harma ta dawo ta koyi rayuwa a haka,...............ita baban abinda ya fi tsaye mata a rai shine shin me ta yiwa maza da zafi haka ne? Me suke nufi to da ita ne? , Shin a matsayinta idan ta dauki dabi'a irin marar kyau yawo da dan gyale hakan zai zamto alkhairi a gareta da ahalinta da al'umar annabi kuwa?, Me yasa ita ta kasa samun wanda zai fito magana ta tsaya tsayin daka har ya kilaceta matsayin mata ba?, Sau biyu magana na yin kwari da ita har Aba ya sani sai dai shuuuuuu kamar an yi tsatsafa an dauke dan kuwa ko yarfin ruwan kafin a fito ya gushe a ido ne, dan mahaifiyar daya tsaf ta nuna ina hadinta da danta? Wannan jiki haka ai ba na zaman karamin yaro bane sai dai tsoho Wani hawaye ne mai zafi ya ringa bin kumatunta, a hankali ta dora hannunta daidai kahon zuciyarta ta shiga ayana kalamai kamar haka' Shin laifin duka nawa ne? Nice ko? Nice na kasa maida hankali nima na yi kwaliya ko an aureni ko?, Nice na kasa tsayawa na yi dinki irin na yan mata ko a kulani ko? Du laifina ne nice nan bana sakewa mazan fuska ko?, Dan Allah Allah ka san nima na samu mai sona ko na samu ciwon dake zuciyata ya bace, domin *DA CIWO A ZUCIYATA* mai karfi ubangijina......' Gannin tana neman kamuwa da cutar cuwon barin kai saboda tunani ya sakata mikewa a hankali ta je ta dauro alwallah sannan ta dawo ta kabarta sallah ta shiga yin nafila Sosai takw hawaye a cikin sujadarta tana ambaton sunnan Allah kamar yadda ta saba, fatanta Allah ya bata miji na gari itama wanda zaya *YANTATA*, Burinta ta samu miji na gari wanda zai sota domin Allah ya riketa domin Allah, ta tabata Allah zai bata itama , a da damuwar bata gigitata har haka, a yanzu da mahaifinta ya yi maganar nan sai ta ji duka kaf hankalinta ya gama tashi 💔💔💔💔❤‍🩹❤‍🩹💔💔💔💔 *DA CIWO A ZUCIYATA* 💔💔💔💔❤‍🩹❤‍🩹💔💔💔💔 _MALLAKIN_ *SAJIDA NIJAR* *FREE BOOK NE* 6️⃣ LITATAFAN MARUBUCIYAR Duk karyar kada Yar mahaukaciya Neman na kaina Bani da zabi Bak'a ce Kutkale Makauniya ce Mage Duk nisan jifa Idan ka raina inda kake Dutse Alkalamin kadarata Bani da zabi Dakika Biyar Now *Da CIWO A ZUCIYATA* *Tallah, tallah, tallah* *SECRET DE LA FEMME DU MANGA* _Gidan Kamshi, Sirrin Manyan Mata, nesa tazo kusa,Amarya ,Uwar gida,Ango da mai gida Har ma da yan mata da samari shin kuna sane da cewa HAJIYA FUSAM ta shirya tsaf domin gwangwaje ku da turarakunta masu dankaran kamshi? Tare Kayan gyaram jiki na musamman ,wanda daga nesa kamshin ki kadai ya wadatar ya isar da sakon zuwanki waje,gidan ki kuwa sai ya zam abun kwatance wajen kamshi, kar na cika ku da surutu bara in fara zayyano su_ Farar Humura Bakar Humura Humura special, humura de bain Humura epicé Lait de nuit Parfums désodorisant Parfums rideau et dras Lait de nuit Alkam Kulakcam *Waɗannan kadan ne daga bangaren turaran ruwa* Gagab, sandal flex, Durot, durus, sandal fleur, tafarce, farce, sandal bangui, sandal, hypotonic sandal, al'ut, coktail creation VIP, Gajiji, Mankaji, turaran wutar labule da cafet, Aba malan, boulettes *Munada bangaren gyaran jiki kamar haka:* mai mai saka santsin jiki, mai mai kanshi, Kayan gyaran jiki mai saka fata ta yi santsi da laushi, kayan gyaran jiki mai saka fata ta yi fari, Sabulu mai saka fata ta yi haske, sabulu mai saka fata ta yi santsi, sabulu mai goge yanayin fata, mai wanda baya saka fari mai gyara fata Sayen na gari mai da kudi gida,sai an gwada akan san na kwarai💃💃 Hajiya Fusam na zaune a kasar Niger domin yin magana da ita kai tsaye tuntuɓi wannan number 97 82 44 94 *SECRET DE LA FEMME DU MANGA* Gidan Kamshi, Sirrin Manyan Mata💃💃💃💃💃 A yanzu da mahaifinta ya yi maganar nan sai ta ji duka kaf hankalinta ya gama tashi, bata da wani sukuni, da kyar ta ji sasauci a zuciyarta har barci ya yi awon gaba da ita Dukkan abinda suka saba yi da sanyin safiya yauma suka gabatar, sai dai babu wanda bai kula da yannayin sanyin jikinta ba har suka zauna dan karyawa Sunna tsaka da karyawar ne aka yi kiran mahaifinsu cewa yar abokinsa ta rasu magidanciya, wannan dalili ya saka shi mikewa ya shirya da gagawa ya fice ba tare da sun samu sun yi zaman na safia ba A sanyaye ta sanar da mahaifiyarta yau ake kafa masu result na exam dinsu da an jima zata je, maman nata ta amince ko dan ta samu ta je ta dan sake, domin itama karfin hali ne take yi bata da karfin jure yannayin KAUSAR Du a nan tsakar gidan suke zaune KAUSAR ta yi wanka ta shige Da kiciniya dai su suke ji, ama babu wanda ya kawowa ransa abinda yake faruwa, haka kuma ta dan dauki lokaci a cikin dakin bayan ba sabonta bane jimawa ana shiryawa har ta fito tana ta sisine kai dan har ga Allah kunya take ji kwalin da ta saka da girarta da ta caje da dan jan bakin nan kar mahaifiyarta da yan uwanta su gane, sai dai ta makaro domin ko kanshin turaran da take bazawa ya fi wanda ta saba dan gigawa hamatarta, na yau mai girma ne, haka da ta duka dan amsar kudin da mamanta ke bata dole suka yi ido hudu har maman nata ta ga kwalin dake saka idon nata hawaye dan bata saba ba, hakan ya sale karyar mata da zuciya ta dauke kai da sauri ta laluba yar karamar jakarta ta ciro dari biyu ta karra mata sannan ta suri bokici ta ce" Idan kin fito daga leka sakamakon ki tsaya gidan Laria ta maki kitso " Kudin ta cure a hannunta ta yi wufff ta fice a gidan cike da tarin kunyar hijab din dake jikinta bai kai mata har idon kafa ba kamar yadda ta saba sakawa, tsayinsa daya da tufafinta Tun tana tunanin zata iya jurewa ta dago kanta har ta sadakas gaba daya ta ja hijabin ta rufe jan bakin tana jin nauyi a ranta kamar ta aikata wani abin kunya Haka ta je ta duba result dinta sannan ta fito ta karasa gidan Laria ta shige suka shiga hirar yaushe gamo aka kwonce kan aka shiga wankeshi bayan ya bushe aka dasa mata kitso wanda zai hau da yannayin gashinta Ita da kanta sai ta ringa jin wani dadi dadi a kan nata, bama da ta je ta yi alwalar sallar azahar haka ta jita sakai ruwa na ratsa dukan kofofin kanta Sai kusan la'asar ta fito daga gidan, haka kawai ta dasa tafiyar kafa, tafia a hankali ba kamar yadda ta saba ba, tana tafe tana tunanin dacewa a cen kasan zuciyarta, a ganninta yanzun kam ga kunshi a hannunta, ga kitso, idonta da kwali daidai gwargwado dai ai kwaliya ta kare ya dace ta samu mashinshinin da zata yiwa Abansu maganar itama ta samo fa, sai dai abin mamaki har ta cinye dogon layin kasuwa ta shiga na gidansu shiru kake ji wai maye ya ci shirwa, a lokacin da ta kawo kan kwana nema ta kusan hadewa da wani dan garuwa kana ganninsa ka san ba yaro bane ya wani ce da ita yi hakuri Mama ban kula ba Ita da abin ya wani daketa ko ci kanka bata ce da shi ba ta ci gaba da tafia zuciyarta na zafi har ta shige gida Ko da ta shiga gidan kasa cin abinci ta yi,mahaifiyarta dama sunna cen kai gara, sai kannenta Rukaya na kicin Aisha na wanke wanke ya wuce dakinsu ta tsuguna cen wata loko ta hade kanta da gwuiwa ta fashe da kukan da take ta rikewa tun a hanya Da sauri Aisha ta dago daga wanke wankenta ta kallo kofar dakinsu, hakama Rukaya dake kada miya da sauri ta kallo wajen Rige rigen shiga dakin suka yi dan kukan na KAUSAR har tsakar gida Gaba na Faduwa Aisha ta duka tana kokarin kama KAUSAR ta ce" Auntynmu lafia? Waye ya saka ki kuka?" Rukaya da tuni ta fara gargadar murya zata fashe da kukan itama ta ce" Auntynmu wani abu ya same ki? Ke da waye kike kuka?" KAUSAR ta yi iya yinta dan ta yi kukanta ita kadai ama abin ya faskara, a dole ta dora kanta a gefen kafadar A'isha tana kukan ta ce" Aisha, na shiga uku, wayo Allahna, A'isha shin menene cutar da maza basa so a jikina? Na zama katuwar budurwa a cikin gida na kasa matsawa da tuntuni kuma kun samu kun matsa?, Aisha ku bar gannin na mayar da hankalina kan karatu ba dare ba rana ni dai karatu nima fa mutun ce kuma abinda kowa ke so ina so, Aisha samuwa ne bai yi ba a dole na hakura na rungumi karatun dan shi baya min tawaye, Rukaya kunna gani in dai aka ce ana sona dan tsokana ne ko dan a batan lokaci, dududu yan matancina bai fi a irga da na hadu da su ba suka nuna na masu, To ni yaya zan yi da raina ne?, Ni babu ruwana da sana'arka in dai na halal kake nema, nagartace mai halin datako nake nema wanda zai rikeni da mutunci nima, Aisha kunna gani habaice habaicen dangi har bana so a yi taron da dole sai mun je dan ta yannayin kallon da ake bina da shi kadai sai in ji du na tsani kaina, domin wasu basu zageni ba ama kallon da ake bina da shi yana fasara abinda aka kule a zuciya a kaina, shin ba za'a fahimci y'ar sunna nake du rashin hankalina ina son raya sunna ba?, Kun ga dai yanzu Abanmu shima hankalinsa ya karkato kanmu, kuma yana fa gaskiya shekaruna nawa bale ku?, Ina matukar jin tsoron na kasa farantawa Abanmu bayan shi rayuwarsa kulun a cikin faranta mana yake , bawan Allahn nan a duniya bashi da damuwar da ta wuce tamu, Rukaya nima ina so na amsa shi idan ya sake mana tambayar nan dan bana so hankalinsa ya tashi a kaina, wayo Allahna ni duka kaf kowama ya tsaneni, na gaza samun tsayaye ? Ku duba ku gani yadda na gandame na gaza samun tsayaye?, Ni komai tsufan mutun ni dai a min auren hankalin su Mama ya kwonta summa, a anguwar nan fa da gangan ake yadawa mamanmu magana kunna kallo, yi take yi kamar bata gane yaren da aka haifeta cikinsa dan a zauna lafia, wai mutane dan rashin jin tsoron Allah basa gane cewa auren nan lokaci ne sai su ringa maka muguwar fasara?, Aisha Rukaya kun san Allah idan har na taba saka iskanci a raina ya hanna min kula namiji da nufin aure Allah ya hanna min dukan farin cikon duniya da kiyama, kun dai ga TAUFEEK ne kadai namiji kwal a duniya da muke kawance zumunci wanda ya gama gari yanzun ba wani abin mamaki bane hakan ko? To ku shaida ne TAUFEEK shine mai min fadan in gyara ba dai ya yarda ya batan ba, kuma a kan mutuncina TAUFEEK sai ya bata da du wani saurayin da ya so zagina dan ni ganau ce ba jiyau ba , ko baban abokinsa da ya taba ce min wai me yasa ni hijab hijab ina boye jiki kamar mai gyambo har gobe basa shiri dan a gabana a gabansa yace bai taba tunanin zai wulakantani ba, ya daukeni kanwarsa kawarsa aminiyarsa ba zai bari a wulakantani ba, kin ga shi dinma jiya na masa rashin kunya ya kyaleni irin jeki katuwar banza ki yi haukanki ko? Shikenan A'isha ni kam duniyar tai min zafi Allah ma kuwa....." A hankali mahaifinsu ya yi baya, ya jima da dawowa anguwar daga wajen jana'izar y'ar abokin nasa, gannin bata dawo ba ya saka shi zama cen wajen mai shayi sunna taba hira yana kuma kallon hanyar da zata bilo, Yana gannin shigowarta da yannayin fuskarta ya taho shine ya iske koke kokensu da magangannunta Ajiyar zuciya ya sauke a soron gidansa ya daga kansa sama a hankali ya furta" Allah kaine Allah, kai kadai ka san abinda ka boye a jinkirin auren y'ata, Allah kai ka halicemu kuma ka bamu jarabawar rayuwa dan ka auna imaninmu wanda zai karra mana kusanci da kai, ya ubangijin al'arshi idanma KAUSAR bata da rabon yin aure a duniya har ta koma gareka ne ni bani da ja kuma nani da matsala a abinda ka kadartawa bawanka, Allah ina rokonka a tafiyarta da dawowarta a mu'amalarta ta yau da kulun ka karra tsareta ka kareta ka hanna dukan wani mugun abin dake iya samunta wanda zai saka mu zubar fa hawayenmu a kanta, ya ubanji ga baiwarka nan idan har tana da rabon yin auren kuwa ka fitar mata da miji mai jin tsoronka, mai ibada, wanda zai riketa dominka ya zamto malami, yaya, amini, masoyi a gareta, da yardarka ba zan kuma daga mata hankali ba, ama zan ringa tuni da maganar auren dan ta ringa kokari irin nata, Allah na gode maka da yau har ta je ta yi kitso mamanta kuma tace harda kwaliya ta yi, ka karra kare min ita a duk inda take....." Adu'ar da ya yi kennan kafin ya fice daga gidan dan zuwa samun liman ya karra amso aduo'i kamar yadda ya saba A cikin dakin kuwa rarashinta suke yi har sai da ta daina kukan ta dawo sauke ajiyar zuciya A tausashe tamkar sunne yayun suka ringa nuna mata cewar kowani bawa ai da irin kadararsa, jarabawa ce ta ubangiji kuma alhamdulilah Allah ya basu iyaye masu tausasawa a dukkan rikita rikitar dake iya samunsu yau da gobe a cikin gidansu Cikin ikon Allah suka samu ta saki jikinta sosai sai ajiyar zuciyar da take ta saukewa kafin A'isha ta dauki wayarta ta buga numbar TAUFEEK bayan tace bara a mata kiran TAUFEEK din ta bashi hakuri tunda da kanta ta gane itace da laifi tace ta masa rashin kunya Kira na farko bai daga ba, sai a na biyu ne ya daga kuma ya yi shiru ya ki ya yi magana hakan ya sa Aisha yin murmushi dan ta san TAUFEEK ba dai zuciya ba ta ce" Yayanmu barka da warhaka, dama bamu jika ba muka ce bara mu tabo mu gaisar da kai" Amsata ya yi jin A'isha ce sai kuma ta ba Kausar wayar tana fadin" Amshi aunty ga yayanmu nan" Wayar ta amsa tana kallonsu sunna dariya suka fice dan yadda ta zaro ido irin kuma sai ki bani? Shiru ya mata kamarma ya ajiye wayar, sai dai ita ta san bai ajiye din ba dan baya mata haka du fadan da zasu yi kuwa Hanci ta ja wani hawayen ya bale mata a sanyaye ta ce"Ka yi hakuri dan Allah" Wani irin tsinkewa gabansa ya yi ya fadi har sai da ya dakatar da rubuta code din bankinsa da yake yin transfer ya saurara yana sake tabatar da kamar kuka take yi kamar kuma mura take, sai dai to me zai sakata kuka ita ? KAUSAR fa mutun ce mai mugun hakuri da kuma juriya, har ga Allah shi yana girmama hakurinta da kawar da kanta a kan abubuwa da dama, kuma ya san dai fadansu ba shine zai saka ta yi kuka ba, shi yasa ya ce" Mura kike yi ne?" KAUSAR ta dan yi jim, Sa kawai ta fashe masa da kuka har tana shasheka ta ce" TAUFEEK...... TAUFEEK ka gani ko?????" Idannuwansa ya rintse a hankali ya idasa saka code din ya tura ya rufe computer sannan ya mike ya kashe kiran ya fito daga office din nasa yana lalubar aljihunsa dan jin inda ky dinsa yake ya nufi wajen dankareriyar jeep dinsa dake ajiye ya bude ya shiga yana dan lalubar gashinsa ya kunna sannan ya harbata kan titi Silalewarya ta yi tana hawayenta, bayan ta yi tunanin gaba yake mata shima ta rintse ido tana tunanin to mema ta masa ai du laifinsa ne ta yi zuru zuru ta jiyo muryar Abansu yana fadin" Shiga mana TAUFEEK, ke Rukaya shinfida masa tabarma , nima ba zama zan ba zan koma nan na dawo" Firgigit ta mike daga kwonciyar ta bi Rukaya da ido da ta fitar da tabarmar ta shinfidawa TAUFEEK wanda ya cire takalminsa ya zauna yana kunce agogonsa ya ajiye gefe kafin ya dago kansa ya zuba mata ido Abinda da mai manyan idannuwa masha Allah idon yai mata zuru zuru ya yi ja , haka abin kwalin du ya zubo sai wani wiki wikitu take da idon tana kikiftawa shi kuwa yana sake kallonta har ta karaso tana kallon A'isha ta janyo masa ruwa a rijiya a zuba a tsaftatacen kwanon silba an ajiye masa Habarta ta ringa sosawa a hankali murya shake ta ce" Da kana anguwar?" Hannunta ya bi da kallo dake dauke da kunshi ja ya dan tabe baki ya ce" Ke kukan me kike, ke da waye?" Kasa kasa ta yarda harara ta ce" 💔💔💔💔❤‍🩹❤‍🩹💔💔💔💔 *DA CIWO A ZUCIYATA* 💔💔💔💔❤‍🩹❤‍🩹💔💔💔💔 _MALLAKIN_ *SAJIDA NIJAR* *FREE BOOK NE* 7️⃣ LITATAFAN MARUBUCIYAR Duk karyar kada Yar mahaukaciya Neman na kaina Bani da zabi Bak'a ce Kutkale Makauniya ce Mage Duk nisan jifa Idan ka raina inda kake Dutse Alkalamin kadarata Bani da zabi Dakika Biyar Now *Da CIWO A ZUCIYATA* *Tallah, tallah, tallah* *SECRET DE LA FEMME DU MANGA* _Gidan Kamshi, Sirrin Manyan Mata, nesa tazo kusa,Amarya ,Uwar gida,Ango da mai gida Har ma da yan mata da samari shin kuna sane da cewa HAJIYA FUSAM ta shirya tsaf domin gwangwaje ku da turarakunta masu dankaran kamshi? Tare Kayan gyaram jiki na musamman ,wanda daga nesa kamshin ki kadai ya wadatar ya isar da sakon zuwanki waje,gidan ki kuwa sai ya zam abun kwatance wajen kamshi, kar na cika ku da surutu bara in fara zayyano su_ Farar Humura Bakar Humura Humura special, humura de bain Humura epicé Lait de nuit Parfums désodorisant Parfums rideau et dras Lait de nuit Alkam Kulakcam *Waɗannan kadan ne daga bangaren turaran ruwa* Gagab, sandal flex, Durot, durus, sandal fleur, tafarce, farce, sandal bangui, sandal, hypotonic sandal, al'ut, coktail creation VIP, Gajiji, Mankaji, turaran wutar labule da cafet, Aba malan, boulettes *Munada bangaren gyaran jiki kamar haka:* mai mai saka santsin jiki, mai mai kanshi, Kayan gyaran jiki mai saka fata ta yi santsi da laushi, kayan gyaran jiki mai saka fata ta yi fari, Sabulu mai saka fata ta yi haske, sabulu mai saka fata ta yi santsi, sabulu mai goge yanayin fata, mai wanda baya saka fari mai gyara fata Sayen na gari mai da kudi gida,sai an gwada akan san na kwarai💃💃 Hajiya Fusam na zaune a kasar Niger domin yin magana da ita kai tsaye tuntuɓi wannan number 97 82 44 94 *SECRET DE LA FEMME DU MANGA* Gidan Kamshi, Sirrin Manyan Mata💃💃💃💃💃 Kasa kasa ta yarda harara ta ce" Kukan me zan yi ni kuwa, ba kukan da nake yi" Da haushi haushi ya ce" Kin ga ya isheki haka, zaki fada min kukan me kike yi ko ba zaki fada ba?" Ido ta zarro tana kallonsa ta ce" Besty dukana zaka yi?" Shima ya kare mata kallon da haushi ya ce" Idan ta kama a dake kin ai option ne, meye wannan a fuskarki du ya maki baki ? " Sai a lokacin ta shafo sai kuma ta tuna ashe fa kwali ta saka itama a ido Daria ta saka kasa kasa tana sake gogewa da kyau ta ce" Malan ya ka ga mata? Kwali na saka kuma na je na yi kitso harda kunshi....." Ta karashe tana wani basarwa ta wani hade fuska irin ta kankaro wulakancin nan Murmushi yake yiwa dariyar su Rukaya dake mata tsokanar wa ya ga ba saban ba A tausashe ya ce" Rukaya kukan me take yi wannan matar? " Rukaya ta kalli auntynsu, ta kalle shi sai ta samu kanta da kasa sanar masa, tunda bata san ko auntynsu zata so hakan ba Itama da basarwa ta ce" Ba fa abinda nake yiwa kuka, ra'ayi ne ai shi kuma kuka kamawa ne" Shiru ya mata dan ya kula banda tashin balagar rashin kunya harda neman fitina a wajen yar nan yau Hira suka shiga yi tsakanin su hudun, duda su Aisha hirarsu ta fi karfi, su hirarsu a kan abinda ya shafi karatun fa ta kirta ba dadi a kai ne da kuma hira irin ta gidansu haka wace dai yawanci abokanai ke yi idan sun hade ne kawai suke yi, yan matan na aikinsu su kuwa sunna zaune har dai hirar ta yi nisa sosai sannan ya tunna abinda yake son fada mata da kula ya sanar mata abinda Abansa ya yanke kan maganar aurensa da YUMNAH wace ta san da zancen dama kuma ta san da an yi zaman ba'a dai yanke bane Farin cikin da ya wanzu a fuskarta sai da ya saka A'isha wace jikinta haka kawai ya yi sanyi tana kallonta dakatawa ta zuba mata ido sosai tana kallonta a lokacin da KAUSAR ke ta murna tana ainahin fitar da murnarta kafin ta ce" Allah na gode maka zan aurar da besty, tsayama wai kennan kwana nawa ya rage? Bai fi arba'in da uku ba fa, gaskiya aiki ja a gabana, kuma tun yanzu zan fitarwa da yan mata da samari anko, ta yan mata daban ta samarin daban du wanda bai min ba ya cira bata nuna ba, ka ga fa azumin da za'a fara jibi da sati saya zamu shiga aji mu yi jarabawar ai ni komai ya zo min daidai ba tunanin jarabawa bale na kasa kwaso shoki dan kuwa sai na kwaso shoki" Ido ya zarro ya ce" KAUSAR shoki? Dama kina rawa?" KAUSAR ta yi dariya tana sakar masa harara ta ce" Komai ai da mafari, a aurenka rawa zan har kafafuwana su yi ciwo, me kake tunani?" Daria ya yi yana girgiza kai dama ya san farin cikin da zata nuna idan ta ji mai yawa ne, gashi ko YUMNAH dinma bai hadu da ita ba bata san maganar ba , domin da ta sani ya tabata da Yumnah ta neme shi ta fada masa Haka dai ya cika dare domin sai bayan magariba ya tafi har Mama ta zo nan fa ta sanarwa Mama maganar auren sai murna take inda mahaifiyarta itama ta tayasu murna har tana fadin" Lalle daga yau ganninki sai an shirya , watau kirjin biki ba dama, kema Allah ya nuna mana naki KAUSAR na tabata har TAUFEEK sai ya gayato mutanen da ba yan gari ba" Daria suka yi gaba dayansu, suka sake cika dare sunna hira kowa ya je ya kwonta A daren ne Aba ya zauna da mamansu ya sanar matta abinda ya yanke, ya fada mata ba zai tayarwa da Kausar hankali ba, zai ci gaba da addu'a, ama yan uwanta a ba manema aurensu damar su turo dan ba za'a ce sai ta samu ba tukunnan a hade Karshe dai da tsokana suka kwonta domin ya shigo da wani katon asusu ya bata kudade yana fadin a zuba a adana masa shi yanzu kuma a dole ya kule ciki ko ya yiwa yan mata gado da gara............ Daga wannan ranar KAUSAR ta daina gannin magana makamanciyar haka, Sai dai tana gannin yan shirye shirye na auren kannenta Haka kuma gefe guda Aisha da Rukaya sun sakota a gaba ga karatu ga jarabawar karshen shekara su a dole sai ta ringa kwaliya tana gyagyarawa irin nasu bayan ita ta san ba zata taba yin irin nasu ba, za dai ta kamanta Wannan jarabawar kaf dinta da TAUFEEK aka yi har karshe, kuma cikin ikon Allah idan aka shiga aka fito suka zauna sunna dudubawa ba laifi ya amsa tambayoyi masu yawa harma ya bata mamaki domin bata yake ta rike ya ringa fada mata amsoshin da ya bayar itama sai ta ga hakan ne ta bayar hakan na nufin ya leka karatun ya duba sosai, sai ta ji nutsuwa a zuciyarta harma ana gama jarabawar da sati daya ta je ita da su Rukaya suka fitar da anko ta maza shada ruwan sararin samaniya , ta mata atampa mai tsada mai kyan gaske mai sirkin ruwan sararin samaniyar da baki baki wace ke iya yiwa kowace fata kyau Daga kasuwar direct gidansu TAUFEEK suka wuce domin sun sanar da Mama cewar idan sun cire zasu kaima mamansa dan sun yi waya tace tana jira idan KAUSAR din ta ciro anko din ta kawo mata kalar da sunnan shagon da aka fitar dan a sayo na jama'ar gidan Kasancewar Azumi ne basu samu matan gidan a falo ba, kuma yau girkin Maman ne sai kawai suka samu Maman suka nuna mata ta yaba sosai sannan ta nemi da su zauna su sha ruwa kafin su tafi, ama suka nuna sun baro Mama da aiki a gida, a dole ta salamesu da kyauta kamar yadda ta saba duda sai da ta kusan kaiwa Kausar rankwashi a kan ta nuna na zasu amshi kudi ba ga wata leda mai dauke da kaya nauyi jikit wai ankon safensu ne, atampar da suka fitar ta rana ce , da jin ledar ta yi nauyi ba iya ankon kadai bane Haka suka fito sunna ta godiya ISHRAT na biye da su tana labari suka nufi bangaren Hajia, domin ko giyar wake ta sha ba zata shigo ta fita bata je ta gaisar da hajiar ba Hajia na zaune saman kafet tana kallon gabas sai musmus take da baki ga dukan alamu carbi take ja dan kuwa tana ta ja tana motsa bakinta ne, dakinta dauke da kanshin turaran wuta ya game ko'ina sai dai yau ba hayakin nan bane mai yawa babuma hayakin kamar yannayin dakin ne da ya saba da kama turare idan bako ya shigo zai ji kanshin ama ita dake ciki ba lale bane kanshin ta ji shi Da murmushi take amsa gaisuwar KAUSAR har KAUSAR ta gama gaisheta a duke sannan ta mike ta zauna kusa da ita kadan tana ciro ankon da hannu biyu ta mika mata ta ce" Hajia, dama daga ciro ankon muke, kin ganshi nan, wannan ne na mata ga kuma na maza nan" Hajia ta saki murmurshi ta karbi atampar, tana daf da yin magana aka daga labulen kuryarta aka leko kadan , hakan ya sa ta dago ta zuba idannuwanta tana kallo hadi da kankance dubanta Baki ta tabe ta cire kai kasa kasa ta ce" Munafurci dai ba abun yi bane, aikin mata du sai kaura yake yi yana sarkafar maza, in ba tsohon munafurci ba ai da na tsaya ina maka magana shiru ka min irin ka yi barci, ama yanzu kana jin maganar ita wannan ka wani leko, uhum zamani mai abin mamaki ku duka bakwa jin tsoron Allah, ace wai iyayenku na kallo ita wannan din itace kawarka kai kuma abokinta, a gaban mai kwanonima sai a zanta, ai tunda yanzu na yarda eh kawancen ne abu daya nake jira na ga na mika ka dakin Yamaniya ita kuma itama dakin miji in ga iya shege, ai nasara ba kowa ya samu galaba a kansa ba, na tabata in kai ka fi karfin Yamaniya ita wannan mijin da za'a aura mata zai fi karfinta, ni abinda na kasa ganewa wai me kike jira har yanzu ba'ai maki aure ba?" A'isha ta turo baki tana ji uwa ta mike ta bar auntynta a dakin nan ta yi tafiyarta, itafa dama tsoron tsohuwar nan take yi sosai, babu wanda ta bari, da ta ji maganar kawancen auntynsu da jikanta shigarta gidan ya fi a irga, har cewa take yi a dai ringa saka ido kar a ringa barinsu su kadai lau a haifo masu dan besty Da kyar ta hakura da zumuncinsu sannu a hankali har take kaunar Kausar, ama hakan baya hana ta ringa yanko zance marar tsari haka kawai Fuska ya daure ya fito gaba dayansa ya kai zaune yan duban Kausar ya ce" Daga ina kike ke?" Hajia ta sake zuba masa ido tana kankancewa ta ce" Daga inda ka aiketa ubanta!" KAUSAR ta zarro ido sai kuma ta dauke kanta tana murmushi ta nuna masa atampar dake hannun hajia ta ce" Ankon muka ciro ka manta ne na fada maka jiya cewa yau zamu je kasuwar? Biyu na raba na hannun nan na wajen Hajiya naka ne ka gwadawa abokananka ni kuwa jibi in sha Allah zan fara gwadawa sauran freinds" Ankon ya dan kalla sai kuma ya yi diffg bai ce masu komai ba, Hajia kuwa har yi take kamar zata bude masu baki ta kalli wannan ta kalli wancen, cen dai ajinta ya tsimkota ta ce" Ni ko a kauye, zamanin da nake ta balarabe, kafin kawata ta kwacen shi karya ne ace a kawancenmu ni in ringa yiwa kawa surutu ta kyale ni, wannan ƙawance naku lalle akoy alamar tambaya, ace kina surutu ya wani kyale ki? In nice in na kumaa kulaka in zama tsintsiyar sharar kurma!" Aisha ta mike tsagal tana tatara komatsansu tana fan murmushi ta ce" To bara na tare mana taxi Aunty "" KAUSAR kam dariyarta take ci, ita fa walahi lamarin hajia baya wani damunta, baya taba bata mata rai, kuma tsufan HAJIA tsufa ne mai kyau, domin koda yaushe tana rike da carbinta tana ja, wannan zamanin da ya zama abin tashin hankali wani tsufan dake zuwa a gigice? Rikicinta kuwa tafe yake da rashin munafurci da bata iya ba, wasu bama tsofin bane a gaban idannuwanka zasu nuna maka so a bayan idannuwanka kuwa tamkar su soka maka wuka su daina ganninka a cikin duniyar kwata kwata Fitowar da ya sake yi da ky a hannunsa ya ce" Tashi mu je" ya saka HAJIA sakin murmushi tana kallonsa ta ce" Ba dai rai na bata maka ba ko? Ai ka ga ciwon kai kake yau kuma kace tare zamu sha ruwan ko? KAUSAR tayani gani kamar ya kumbura fuska?" KAUSAR ta girgiza kai tana murmushi ta ce" Hajia yama yarda ya maki fushi haba dai, bai yi fushi ba ko besty?" Gannin ba dai zata tashin ba ya saka shi yin gaba , hakan ya sa ta mike da sauri, hajiarma ta mike tana fadin" Bara in dubo maki yar tsaraba Y'ar nan, yadda kika san me bana iya na ganki ban dan miko maki wani abin na tsaya tsaya ai na zai tafi ya barki ba" KAUSAR na faman Hajia dan Allah ki barshi na gode Allah ya saka da alkhairi ama sai da ta fito da bak'ar leda tana murmushi ta ce" ke kuwa, sakon Babanki ne duda yau bai aikon da goron ba, ki ce ina gaishe su kin ji? Allah ya maki albarka" Amsa ta yi bayan ta rage tsayinta sannan ta ringa godiyar itama ta fice ta fito tana ta waige dan gannin inda zata ganshi Da sauri ta karasa wajen motar yar sumulmula fara dake parker ta bude gabam ta shiga ta rufo tana fadin" Ka ga fa da bari ka yi muka shiga taxi kai dake ciwon kai?, Wai ciwon kan menene haka?" Hanci ya dan ja kadan yana tashin motar ya fara tafia da su a hankali ya ce" inaga rashin isashen barci ne, shi yasa yau ban fita ba na huta" Kai ta gyada ta ce" Banama kana jan tafsir ne?" Kai ya gyada kawai bai bata dogon amsa a wannan tambayar ba, sai kuma ya ce" A wani shago kika fitar da ankon nan?" Dan murmushi ta yi ta ce" a shagon Elhaji Habu ne, ana mutumen nan bashi da kirki kawai sharin mutane ne, mu dai ya mana mutunci sosai" Baki kawai ya tabe har suka karasa gidan bai kuma cewa komai ba sai tatausan karatun dake tashi a hankali a cikin motar A kofar gidan suka tsaya Aisha ta ringa sauke kayansu murna fal zuciyarta tana kaiwa ciki sannan ta dawo ta dan rage tsayi tana yi masa godiya ina ya zabga mata harara ya ce" Malama mike ki bace min da gani ni" Da daria ta mike din ta yi ciki KAUSAR da kula ta kalle shi ta ce" Kamar ranka a bace ko ciwon kan ne?" "Na gaji ne" ya bata amsa , sai kuma ya kalli agogo ya kalleta zai yi magana ta sake fadin" Ko na fadawa Mama ta maka kunun ayar nan? Na ga kamar kana sonshi?" Ido ya zarro da sauri ya girgiza kansa, wanda hakan har ya so dan bata mamaki, sai kuma ya cire mata mamakin ta hanyar fadin yau ba zai fito ba zai je makaranta ne, a zuciyarsa kuwa yana ambaton ina shi ina kunnun nan? Abu dadi a baki yana sha kamar kar ya kare ashe ashe yana shirya masa tashin hankali ne? Saboda kunnun ayar nan da ya sha jiya a gida ya gaza barci har kusan biyu na dare yana fama da ciwon ciki, ga tarin gajiyar kasuwa da ta huldodinsa na gida da waje, a haka a dadafe ya kai kiran sallar fari , an yi kira kuwa ai ba barci dole ya sake fitowa ya sha madara mai dumin gaske har yana zufa, shi dai ya rainawa kunnun aya wayo kuma ya yi tirrr da shi dan bai kyauta masa ba Gannin yau kamar yan shiru shirun sun fi komai yawa ya sakata yi masa salama ta yi shigewarta gida tana cire hijab dinta tana shafa cikinta da yake ta sabewa saboda abin azumi a jikin nata shi kadai ke raguwa sosai sanadiyar azumi ama ba wai shafewar dindindin ba, dama da azumi haka yake mata yakan ragu sosai, har bayan azuminma yana iya daukan kusan wata biyu bai koma yadda yake ba, sai fatar jikinta dake dan karra gyaruwa daga yannayin haskenta kadan ta karra yin luwaiwai, ko dan zaman gida ne da hutu ba hanyar school?, Itafa ba fa fara bace aa, fatar mahaifiyarta ce mai haske haka, irin bakin nan mai haske mai kyau, to haka yannayin fatar jikinta take "KAUSAR, wannan kaya haka jama'a mutanen nan su basa gajiya da dawainiya ne Fisabililahi?, Shin auren yaron nan ni me zan yi na kyautatawa ga ahalin nan?" RUKAYA dake ta farin cikin itama domin sun zagaye kayan sunna ta dadagawa ne ta ce" Mamanmu, sai dai a je tunda safe idanma da hali a kwana a cen ko kwana biyuma , in ba wannan ba ina muka ga abin basu?" Mama ta yi murmushi ta ce" Gaskiya ne daurin aure har amsar amarya da mu za'a yi shi, ama kuma du yawan arzikin mai arziki yana jin dadi idan ya ga an masa kara an kula, in sha Allah komai kankantar bajintarmu zaki ga mahaifiyarsa da shi kansa sun ji dadinta, duba fa ki gani, idan ta tashi ware mana abu harta ni sai an ware nawa , lalle zumuncin mace da namiji akoy jin wani iri, ama idan har da kare dokokin Allah sai nace na Kausar da TAUFEEK alkhairinsa muke gani, idan an yi aure kowane ya kama gabansa kuma shikenan sai zumuncin mu iyaye in mun rike" KAUSAR ta yi murmushi tana kaiwa zaune hadi da neman wajen kwonciya ta ce" Mama, yinwa nake ji" Mama ta dungure mata kai ta ce" Zaki fara ko?, Ke kam ki yi kokari ki daina yiwa ciki bauta, wannan lamari naki da cikinki abin haushi, ace mace kadan ta ji yinwa ta kama raki kennan?, Azumi dai baya son haka, tashi maza yau ke zami tuka tuwon sahur kin ga na shinkafa za'a tuka kuma kin fimu iyashi" Baki ta zumburo ta ringa kyakyafta ido tana jin gaba daya kasala da juwa sai yanzu suke lulubeta, ama a haka dole ta mike ta kama aikinta dan kuwa kowa da aikinsa basa barin Maman ta yi komai har a sha ruwa sai iya aikin Baba wanda har yau suke mamakin irin yadda Mamansu bata sakar masu aikin mahaifin nasu, lokuta da dama idan sun yi nacin hakan sai tace to ita kuma a ina zata samu ladan ? Kowa ya yi inda yake da lada kawai su barta da aikin mijinta (wannan din wata hikima ce da hanyar da zaka iya ba yayanka tarbiyyar sanni da kuma sake rike girman miji a bayyane da kuma badini, domin a rayuwa yaya babu abinda ya kai iyayensu girma da daraja, sukan dauki dukkan abinda iyayensu suka dauka da daraja suma da daraja ne, idan har uba na so ya'yansa su raina shi ko su ringa yi masa biyayar dole to ya ringa wulakanta mahaifiyarsu a gabansu , a cikin iyayen kuwa wace ta fi gagawar saka zuciyar ƴaƴanta biyaya da daukan launin abinda take so itace uwa, uwa idan ta so za'a gyaru, in ta ki za'a lalace kuma a kan turbar da ta dora ne, Muna karbe du wani motsi na iyayenmu muna hanna su yi dan ba zamu iya muna zaune su motsa su yi wani abin ba bayan gamu a zaune, hanyar da suke bi ta nuna mana na mahaifinmu bamu da hurumi a ciki na matukar shiga zuciyarmu har muma muna gina tamu rayuwar a haka, idan har a gidan aure irin haka ta samu kuwa inaga da izinin mai sama jin dadin zaman auren zai samu domin akoy gannin kima da biyayar wanda ya ajiyeka...., Allah ya dafa mana) A lokacin da Baba ya zo aka sha ruwa aka wuce masalaci sai kusan goma suka dawo suka zauna fan cin abinci, a kuma lokacin ne Aisha da zumudinta ta kawowa Baba kayan 💔💔💔💔❤‍🩹❤‍🩹💔💔💔💔 *DA CIWO A ZUCIYATA* 💔💔💔💔❤‍🩹❤‍🩹💔💔💔💔 _MALLAKIN_ *SAJIDA NIJAR* *FREE BOOK NE* 8️⃣ LITATAFAN MARUBUCIYAR Duk karyar kada Yar mahaukaciya Neman na kaina Bani da zabi Bak'a ce Kutkale Makauniya ce Mage Duk nisan jifa Idan ka raina inda kake Dutse Alkalamin kadarata Bani da zabi Dakika Biyar Now *Da CIWO A ZUCIYATA* *Tallah, tallah, tallah* *SECRET DE LA FEMME DU MANGA* _Gidan Kamshi, Sirrin Manyan Mata, nesa tazo kusa,Amarya ,Uwar gida,Ango da mai gida Har ma da yan mata da samari shin kuna sane da cewa HAJIYA FUSAM ta shirya tsaf domin gwangwaje ku da turarakunta masu dankaran kamshi? Tare Kayan gyaram jiki na musamman ,wanda daga nesa kamshin ki kadai ya wadatar ya isar da sakon zuwanki waje,gidan ki kuwa sai ya zam abun kwatance wajen kamshi, kar na cika ku da surutu bara in fara zayyano su_ Farar Humura Bakar Humura Humura special, humura de bain Humura epicé Lait de nuit Parfums désodorisant Parfums rideau et dras Lait de nuit Alkam Kulakcam *Waɗannan kadan ne daga bangaren turaran ruwa* Gagab, sandal flex, Durot, durus, sandal fleur, tafarce, farce, sandal bangui, sandal, hypotonic sandal, al'ut, coktail creation VIP, Gajiji, Mankaji, turaran wutar labule da cafet, Aba malan, boulettes *Munada bangaren gyaran jiki kamar haka:* mai mai saka santsin jiki, mai mai kanshi, Kayan gyaran jiki mai saka fata ta yi santsi da laushi, kayan gyaran jiki mai saka fata ta yi fari, Sabulu mai saka fata ta yi haske, sabulu mai saka fata ta yi santsi, sabulu mai goge yanayin fata, mai wanda baya saka fari mai gyara fata Sayen na gari mai da kudi gida,sai an gwada akan san na kwarai💃💃 Hajiya Fusam na zaune a kasar Niger domin yin magana da ita kai tsaye tuntuɓi wannan number 97 82 44 94 *SECRET DE LA FEMME DU MANGA* Gidan Kamshi, Sirrin Manyan Mata💃💃💃💃💃 Sosai Baba ya rasa bakin magana, sai dadagawa yake yi , Shi dai namiji ne bai san tsadar kayan mata a ido ba, in ba zuwa siya ya yi ba yakan hanki masu irin nauyi a idon nan haka a cen bangaren manyan kaya, bangaren abinda ya haura dari du kwaya daya, a yanzu haka wannan na hannunsa ya tabata kudi ne na mamaki, hakan ya sa ya dubi iyalinsa ya ce" Mamansu, kayan nan basu yi yawa ba kuwa?, Kayan nan da gani zasu yi tsada" Murmushi ta yi tana dan sake ziga masa kunnun dake hannunta ta ce" Ai kama Abansu kayan nan zasu yi tsada sosaima, kuma ka ga na wajen mutuniyarka? Har cewa ta yi yau ko dan goron baka aika mata ba, dama jira nake yi idan ka zo ka gani abinda kace sai a yi in sha Allah " (not, kar ki ringa nunawa namiji a cikin gidansa a irin girma da daraja da Allah ya masa cewa bai isa da wasu manyan decision na cikin gidansa ba kece kika isa..., Tsakaninmu mu mun sam cewa muna da baban iko da rayuwarsu fiye da tunanin bawa, domin muna da damar tankwasa su a lokacin da su da kansu basu gane ba....., Yarda da hikima irin tamu ta siya mana haka ba nuna isa da takama ba, to wai wace isarma Allah na tuba ke da akace ki zo ki yi biyaya dan neman aljannarki? Ba gazawa bane dan kin bashi damarsa a matsayinsa na mai nemo gero da hatsi yana daukan decision din abinda ya shafe ku a cikin gidansa.......hakan ba yana nufin ki kasa juya abinki cikin hikima ba, cikin hikimar kina iya samun abinda kike so shima yake so ba tare da daya ya ga an tauye daya ba......, Allah ya karra hada kawunnanmu da Mai hause🥹😍) Murmushi Aba ya yi yana girgiza kai ya ce" Hajia hajiar shagali, ai zan je da kaina na kai mata goronta , ama kuma ba za'a mayar da kayan nan ba, a tsakaninmu da mutanen nan inaga idan muka yi haka bamu kyauta ba, sai dai kin ga kudin shadar da na ba Elhaji? Zan koma na ce zasu je su zabo maku takalma da kudin, idan ya so kudaden takalman da wasu tanadin sai na karra mu fara shirin gudunmuwa, har sai na shiga tunanin nawa zan tanada ta gudunmuwa ?" Mama ta miko masa kunnun da dan dumi ama kuma ba sosai ba tana murmushi ta ce" Abinda Allah ya hore maka, yadda ba zaka takura ba ba kuma zaka yi kauro ba, kai da kake da bikin a gabanka kaima?" Ai kam ta saka shi dariyar, domin katon asusu ne ya bude yake jefa tanadi kulun ta Allah, da safe da kuma yama , tanadin da suke sakawa a tare domin itama in cenjin kayan miya aka yi sai ta kai ta zuba, a zaunen da take yan saide saidenta su lalle da salatif da dai dan abinda ba za'a rasa ba ta kayade riba na hawa tana zubawa, danma ya ki sana'ar a fita ne ai da samun ya fi haka.....haka dai suka cika darensu kafin suke kwonci dan murnar yau ta hanna masu kwonci da wuri Kwana biyu tsakani Khausar ta shiga rabon anko ita da yan uwanta Kusan abinda ke ba Kausar mamaki har ya bata dariya shine du wace ta kaima sai ta jefo mata tambaya fuska cike da mamakin wai dan Allah dama irin yadda zumuncinta yake da TAUFEEK ba saurayinta bane?, Har sai da ta gaji da bada amsar a tsare sai kawai ta katse amsar ta badata a hade dan maganar ta wuce, takan yi dariyar wannan kwabin da wani tunanin wasu mutanen, kai du wanda yake irin wannan tunanim ta yi waje ta ajiye shi a matsayin mutun mafi rashin fahimtar rayuwa gaskiya In ba rashin fahimta ba ina mahadi? Ina hadi? , Eh lalle TAUFEEK ba wai ta girmeshi bane, haka kuma a yannayin jikinsa TAUFEEK ya fita tsayi kuma jikinsa kakauran jiki ne ba lange lange ba, ama sam bata gannin wata mahada ko kamanin dale iya sakawa mutane wannan banzan tunanin, ba wai da tana y'ar talakawa ba yana ɗan masu kudi ba, ko daya, ita bata taba raina asalinta da samun mahainfinta ba, kuma ta san masu kudin na auren talakawan su kilace cikin hukuncin mai sama, abinda ta gama sani ne ko giya take sha TAUFEEK ba abokin soyayarta bane, ba kuma abokin kalamai ire iren wadinnan bane, kai mtssss haka kawai ana nema a hade mata tunani? Tana zamanta ana hade mata lisafi? A gaskiya abin sai ya fara bata haushi da tarin dumbin uban mamaki..... karshe ta kawo na mujiya ta zubawa du mai mata kallon, in har a ganta da ankonsa ba zai cire tambayar nan ba a ran mutun to dan Allah ya rike tambayarsa a ransa abinsa Yawan zuwa shagon Elhaji amsar atampopin masu hada mata kudadensu wata halaka ta kulu a tsakaninta da baban yaron Elhajin watau Mujaheed Alaka ce irin ta shanshakai ta siyaya da farko farko, a hankali ta ringa karantar wasu sababin hulda a tare da shi da suka so bata tsoro, domin sai take tunanin cewa ta zo ne zata yi lokaci kalilan a shagonsu zai kula alakar dan ya tozartata ko dan ya mayar da ita costoma a wajensu ta yadda ko zuwa gaba bata da wajen cire anko sai shagonsu A hankali kiran dake shiga tsakaninsu ya dan fara yawa, ya zamto ya fara sakata boyewa idan har zata amsa kira a cikin gidansu domin kamar jira ake yi yar rakani masai dinta ta kwashi tsuwa du sai a ratabo mata ido ba ga Maman ba , ba ga ya'yan maman ba, uwa uba ana daf da shan ruwan kwana na goma sha takwas da azumi a ranar Aba ya dawo da wuri wayar nan ta dauki tsuwar da ta saka yayan hanjinta yamutsewa dama ga abin yinwa na sakata juwa domin a irin lokacin nan du wani kayan buda baki a gabanta suke jira kawai take yi a yi gyaram murya a masalaci ko na tsokana ne ta daga ta maka sai kawai kiran nan ya shigo ya zamana Aba dake zaune saman darduma yana jan carbi sunna dan taba hira da Mama dake zaune daga kusan dakinta Auta a saman kan cinyarta ya yi matashi yau azumi yake kamar an summar da shi , su Aisha kuwa sunna gama wanke wanke dan su kam da sauki sosai sunna da juriyar azumi sosai da sosai kowa ya juyo inda wayar ke ajiye tana kuka irin na kashe kunnan nan tamkar mai son saka kurma ya ji tana ringin daf da yasashen hannun Kausar dake yashe ya sake du ya fice a hayacinsa Da sauri ta dauke kanta, har zuciyarta bugawa take yi, wani takaici na neman kunnota gannin sunnan dake kai watau ATAMPA sai ta ji kamar tana dagawa ta kirta masa Alllah ya isa da masa tsakani da ita, to in ba yana neman sakata a halin ha'u'i ba a gaban Aba? Sai dai kashhh, a dole hawaye suka tsinke mata a lokacin da Aba cike da wani yannayi na son ta daga wayar ya ce" KAUSAR ba kiranki ake yi ba?" Kai ta girgiza da sauri tana share hawayen dake sake zubo mata murya a kurya ta ce" Ba kira bane Aba" Aba ya kafeta da duba kadan yana fadin" Aa, kamarya ba kira bane, daga mana wannan na uku ne fa, kukan meyema kike ni ba an kusa shan ruwan ba? Ko yau juwar da karfi ne?" Kai ta sake gyadawa , ta dauki wayar ta mike da kyar ta shige ciki ta je cen bayan katifar Mama ta duka ta labe sosai murya a shake ta amsa wayar tana cicijewa da son sannin wani bakon munafurci ne wai wannan kiran nata ba lokaci? Murmushi Mujaheed ya yi , da yannayinsa na sanyi sosai ya ce" Wai kina jin kishirwar nan ta yau kuwa Kausar?" KAUSAR sai ta so ta ce da shi Ina ruwanka da kishirwata? Ni fa bana son neman fitina ban iya fada ba gaskiya, sai dai jin yana dan murmushi ya sake cewa" To ko dai aikin mamana kike ne na dameki?" Ya sakata jin ba zata iya fada masa hakan ba, hasalima sanyin da muryarsa ke yi in zai mata magana na damunta lokuta da dama, sai ta ji kamar ta dauke shi ta goya ta bashi hakuri kar ya yi kuka, kamar wani maraya gaba da baya, koda yake Mujaheed ai bashi da alamun karfima bawan Allah, jiki ne da shi sosai kuma bashi da tsayi, ga yannayi irin na yayan madara dai tare da shi dan ko a shagonsu a zaune yake abinsa yana yan ciye ciyensa yana kai karshen yayan banki, watau shi ke amsa ya ja gaban table ya zuba ya dadana abin irge ya watsa , su kuwa yaran shago na zubawa a leda da kuma kaima mutun waje, sai dai ba zata yi karya ba a dan tsanin zuwa da dawowa sun kula shegen kyauta ne da shi sosai, bayan ribarsu ta atampa da ake ware masu a shagon du wanda ya je siya wace aka basu damar dorawa, sai kuma ya karra masu da na adaidaita sahu du idan sun je , ita tana kyautata zatonma Aisha ko Rukaya yake so, ai kuwa zata fada masa gaskiya ya yi hakuri an masu miji dan har an zauna da manema aurensu an basu su har an saka lokacin biki da babar sallah ne in sha Allah Dan gyaran murya ta yi ta ce" Ina yini Elhaji?" Murmushi ya sake yi ya ce" Lafiya Hajia , yaya gajiya?" Yanzun kam bata amsa ba sai dan uhum kawai da ta ce tana dan murja yan yatsunta, haka kuma wayar na dan tsut tsut tsut alamun wani kiran na shigo mata ne A hankali ta ce" Dama , dama babu mai son atampa fa" Dan tsai ya yi ya ce " Wace atampa fa HAJIA?" KAUSAR ta yatsine gaban goshinta ta ce" Na zata dan ka ji ko na tara kudaden masu son atampa ne?" Har ga Allah abin sai ya bashi dariya, ama sai ya ki nuna mata dan kar ta ji ba dadi, a sanyayensa shima ya ce" Aa, ba wannan bane, dama ji na yi ina matukar son jin muryarki da kuma jin ko kina lafiya? Bale yau kin ga ana rana sosai ga zafi ina jin kishirwa sai na damu da son jin kar aje kema haka kike ji?" KAUSAR ta yi tsuru tsuru, wannan wani irin bakon balagagen tashin hankali ne? Tana zaman zamanta yace wani dan ya ji ko tana lafiya ne? To ita ina hadinta ina shi dan Allah? Mema ta masa da zafi? Da sauri ta samu kanta da kashe wayar tana ta zazaro ido cike da tsoro da fargaba, sai kuma ta ji alamun motsi hakan ya sa ta juyo da sauri Ido hudu suka yi da A'isha, wace tun shigowarta take tsaye tana kallonta da sauraronta Cikin dabara Aisha ta wayance ta ce" Aunty, baki ji kiran sallah bane? Aba yace ace maki an sha ruwa" Sai a lokacin kunnayenta suka ringa jiyo mata alamun dake nuni da an sha ruwa Jiki ba karfi ta mike ta fito ta samu waje ta rakube ta dauki kayan shan ruwanta ta shiga sha tana sauke ajiyar zuciya, baki daya ahalinta sai suka yi tamkar basu ga komai ba suka ci gaba da shan ruwansu suka tayar da sallar magariba Da dare bayan an dawo daga masalaci yau yan matan kaf dinsu sunna daki, tunda yayarsu ta shige ta labe suka tatara abincinsu suka bita, hakan ya sa Abansu dan damuwa yana tambayar wai ina suke ne? Murmushi kawai Mamansu ta yi tana sada kanta, domin har ga Allah ita din da kanta sai ta ji tana iya jin kunyar maganar nan da Abansu, KAUSAR fa itace yarsu ta fari, sai ta ji tana iya jin nauyin maganar sosai da sosai Daria Aba ya yi, har cikin zuciyarsa wani farin cikin na sake ratsa shi, a hankali ya daga hannayensa ya ce " Allah kai ke badawa, kai ke hannawa, ko waye yake son shiga rayuwar y'ata idan da alkhairi ya zo ya ubangijina ka tabatar mana, in ba alkhairi ya zo ba ka rabata da shi cikin aminci, domin irin wahalar zaman da ta sha ina fata idan ta shiga gidan aure ta yi zama na farin ciki" Mama ta amsa da amen a hankali, a zuciyarta kuwa tana tunanin lalle lalle sai ta bada gudunmuwarta itama a matsayinta na uwa, domin ƴaƴanta ita ta haifa babu wace bata san halinta ba, a cikinsu tsaf zata iya zana halayar kowace, ta sani ne bakon lamari ne wannan din a duniyar yarinyarta, idan aka yi wasa tana iya kabe shi ta kore dan tana tsoro, a dole za'a jata a jiki cikin dabara a ringa kwatanta mata har ta gane ta kuma dauka da hannayenta bibiyu ta rike, dole za'a tayata idan ya so in har abin ya tabata gaba sai ta kwaci kanta, sam sam KAUSAR bata da wayon iya zancema bale wai har a kai ga fahimtar junna ita da namiji, zata iya cewa maza biyun nan kwarara sunne suke da mu'amala ta fahimta a tsakaninsu da halayan KAUSAR, daga Abanta sai amininta Da wannan farin cikin suka yi zama a ranar Yan matan kuwa a ciki kowace dariya ke neman halakata Kiri kiri auntynsu ta kashe waya ta nemi mutsukets tana ta hada rai, ta ki kowama ya kawo mata wata maganar ta raini ta hade ta tsare tana ta basarwa, abincin kansa yau ba damka ta sako da sako akai masa ba, sai da aka raba shi biyu sannan aka samu ya shiga a hankali, daga karshema ta yi kwonciyarta da wuri wuri bayan ta kawo dalilinta na kwonciyar da wuri cewa tana so idan Alllah ya wayi gari lafiya su fita da wuri dan kaiwa mace daya da ta rage, tana kuma yarda da maganar Rukaya da tace da ita ya dace su malaki wayar android koda daya tak ce, domin da da ita da ta wayar zasu raba ankon ba tare da sun sha wannan uban yawon ba, abinda ya fi bata takaici da shi kiri kiri ya ki ya rabawa abokanansa maza, sai da ta ga ba fa zai yi ba ta kaiwa amininsa daya da suke jin maganar junna ta bashi ta yi tafiyarta, ta tabata shi kam ya raraba, TAUFEEK kuwa dole ya shafa mata lafiya domin biki sai ta warwasa yadda ake yi a ko'ina ehe! Tsakanin wannan lokacin zuwa karshen wata mai albarka, watau watan azumi a hankali shakuwarsu ta fito fili har ya zamto babu wanda bai san cewa Kausar itama ta samu masoyi ba, ciki kuwa Harda TAUFEEK A hankali yan uwanta suka fi karfinta suka saka mata ra'ayin amsa kiran da kuma ra'ayin kulashi har ya zamto ita da kanta tana jin dadin hakan har ta iya rike lokutan da yakan kirayeta su zanta, sannan ta sanar masa ya yi hakuri nacin yana son zuwa gidansu ya bari a salace baki ya bude sai ta sanar a gida , a lokacin kuwa tuni Mamansu ta sani itacema ta ce sai baki ya bude dan a yanzu cikin ibada ake ba ji ba gani du wani mai neman duniya da kiyama zai maida hankali in dai yana da hankali kuma yana da rabo 💔💔💔💔❤‍🩹❤‍🩹💔💔💔💔 *DA CIWO A ZUCIYATA* 💔💔💔💔❤‍🩹❤‍🩹💔💔💔💔 _MALLAKIN_ *SAJIDA NIJAR* *FREE BOOK NE* 9️⃣ LITATAFAN MARUBUCIYAR Duk karyar kada Yar mahaukaciya Neman na kaina Bani da zabi Bak'a ce Kutkale Makauniya ce Mage Duk nisan jifa Idan ka raina inda kake Dutse Alkalamin kadarata Bani da zabi Dakika Biyar Now *Da CIWO A ZUCIYATA* *Tallah, tallah, tallah* *SECRET DE LA FEMME DU MANGA* _Gidan Kamshi, Sirrin Manyan Mata, nesa tazo kusa,Amarya ,Uwar gida,Ango da mai gida Har ma da yan mata da samari shin kuna sane da cewa HAJIYA FUSAM ta shirya tsaf domin gwangwaje ku da turarakunta masu dankaran kamshi? Tare Kayan gyaram jiki na musamman ,wanda daga nesa kamshin ki kadai ya wadatar ya isar da sakon zuwanki waje,gidan ki kuwa sai ya zam abun kwatance wajen kamshi, kar na cika ku da surutu bara in fara zayyano su_ Farar Humura Bakar Humura Humura special, humura de bain Humura epicé Lait de nuit Parfums désodorisant Parfums rideau et dras Lait de nuit Alkam Kulakcam *Waɗannan kadan ne daga bangaren turaran ruwa* Gagab, sandal flex, Durot, durus, sandal fleur, tafarce, farce, sandal bangui, sandal, hypotonic sandal, al'ut, coktail creation VIP, Gajiji, Mankaji, turaran wutar labule da cafet, Aba malan, boulettes *Munada bangaren gyaran jiki kamar haka:* mai mai saka santsin jiki, mai mai kanshi, Kayan gyaran jiki mai saka fata ta yi santsi da laushi, kayan gyaran jiki mai saka fata ta yi fari, Sabulu mai saka fata ta yi haske, sabulu mai saka fata ta yi santsi, sabulu mai goge yanayin fata, mai wanda baya saka fari mai gyara fata Sayen na gari mai da kudi gida,sai an gwada akan san na kwarai💃💃 Hajiya Fusam na zaune a kasar Niger domin yin magana da ita kai tsaye tuntuɓi wannan number 97 82 44 94 *SECRET DE LA FEMME DU MANGA* Gidan Kamshi, Sirrin Manyan Mata💃💃💃💃💃 Sanu sanu azumi ya zo karshe, aka wayi garin sallah, sallar musulmai, baki daya musulmai kwonsu da kwarkwatarsu a wannan rana sunna cikin yannayi na farin cikin gannin sun samu gabatar da ibadarsu har Allah ya nuna masu ranar sallah Hakan ya sa a ranar da yawa sunna gida wasu kuwa sun fita ziyara...., Ranaku a kalla sun kai biyar da ake gabatar da bikin sallah kennan a kasarmu ta hausawa, ziyara ne gidajen yan uwa da aminan arziki, zuwa wajen wasan sallah ne da sauransu har kwanakin kaiwa samari kwarya kwaryar sallah ta zo, ya kama daidai da ranar da KAUSAR zata amshi nata bakon, watau goma ga watan sallah Ita dai du gannin abun take yi wani iri, bama da ta ga mahaifinta ya shigo da kankana da yan kayan hadin da ya saka Mama ta zana masa ya ba su Aisha kan su yiwa bakon ruwan tarba wanda hakan ya matukar sakata sake jin kunya da nauyin mahaifanta harma ta kashe wayar ta boye a daki ta wuni cikin tunanin ta inama zata fara ? Yaya zata dubi abin? Ta ina zata bi da abin? Haka dai ta har magariba ta kawo kai Mama ta shigo ta tasheta tana fadan me take haka bata kimtsa ba bayan ta san tanada bako? Aisha ce ke dan murmushi tana kallonsu Maman na tsaye kofar bayi tana fadin maza ta yi wankan nan da kyau ta fito Rukaya kuwa ta idasa kimtsa kayan tarbar bakon ta saka a dakin Mama ta kilace bayan sun fitar da na gidan Shirin ya zo mata wani iri, riga da sket dinta sai hijab wanda da kadan ya zarce gwuiwarta aka bata kan su zata saka domin tarban bakon Ta saka sket da rigar ama ta kasa saka hijab din har Rukaya ta sanar da ita cewa bakonta fa na waje kusan minti ashirin kennan Jiki ba karfi ta mike ta dauko wani hijab din sabo wanda suka saka ranar sallah ta zumbula abinta sannan ta dauki carbi kamar wace zata he bayar ta wa'azi ta fito tana rakubewa wayarta a kunnenta tana amsa kiran TAUFEEK dake sanar mata zai biyo ya bata katinta da zata bayar dan ta nace sai da ta buga mata kati na gayata ta samu ta wuce a gidan da kyar tana sauke ajiyar zuciya Motar ta kurawa ido bayan ta ja ta tsaya a kofar gida, ance ta je ta shigo da shi ne, sai dai bata tunanin in har zata iya karasawa wajen motar cen dake tsaye ko ba zata iya karasawa ba, uwa uba yau anguwar dinke take tak da jama'a yan matan ne da samarinsu, tsofafin ne ana firar dare dai haka, kuma a hasken farin watan da ya haske anguwar tarin bolar dake zube ko'ina ta hasku tarrr haka itama ta hasku cikin farin hijabinta harma aka fara dan tsunguri tsoman ana raraba maganar cewa ta yiwu wanda ya saba zuwa ne ko kuwa menene wannan? Ciki harda yan matan da suka sha kwaliya suke kannan bayanta sosai sunna zaune a nasu gefen sun zubo ido sunna son gannin ya fito ya shiga cikin shigarsa ta kamala da tarin kwarjininsa kamar yadda ya saba, sai dai yau har yanzu babu fito daga motar ba Tana kokarin neman layinsa ta ga ya bude motar ya fito, hakan ya sa ta dan sake matsawa kadan jikin garun ta sada kanta "Barka da warhaka Hajia Kausar" ya fada da muryarsa mai sanyi kamar yadda ya saba yi mata magana Cike da kunya ta dan dube shi, sai ta ji inama zata iya rage tsayinta koda basu zo daya ba ta dan gota shi kadan? Sai dai har ga Allah bashida tsayi ko kadan Mujaheed, dan dai yanada dan fadinsa ga tumbinsa kuwa a cikin manyan dinkinma ana gannin yadda ya yi gefe abinsa Dan rage tsayi ta yi ta gaishe shi sannan ta sanar masa ance ya shiga ciki Kwarai ya ji dadin haka, dan hakan ya nuna masa yana iya samun karbuwa wajen iyayenta, domin in har aka baka dama ka shiga cikin gida to fa ana da niyar dubanka ne Har kasa ya duka ya gaisar da Mama dake labe daga daki sannan ya zauna saman tabarmar da aka shinfida masa, ita kuma ta labe daga fan lungun dakin su Mama tana ta aukin murza hannayenta Su aisha sun gaishe shi sun kuma kawo masa ruwa sannan suka basu waje Shiru wajen ya dauka, tamkar bata taba magana da shi a waya ba, kanta a kasa sai zufa take yi, haka yannayin da take ta motsa jikinta na alamun rashin sabo da zama irin haka da namiji ya bashi mamaki Murmushi ya yi ya ce" KAUSAR, alhamdulilah, na godewa Allah da ya nuna min wannan rana, ina ta fata na ganta da raina da lafiyata, sai gashi na ganta, KAUSAR ni di ba yaro bane, inada mata biyu da Y'ayana bakwai, kamar yadda kika ganni a shagon gidanmu shagon mahaifina wannan itace sana'ata, watau ni dan kasuwa ne, a gaskiya ban cika jan neman aure ba dan in har na nuna ina so din nakan fito a mutun a bani na kilace, ni dai na ga kin min kuma ina sonki da aure, dan haka me kika ce ne ke KAUSAR?" Magangannunsa ba da tashin hankali yake fadarsu ba, hasalima a sanyaye harufansa suka fi fita sunna shiga cikin kunnayenta, sai dai mamaki mai karfin gaske da ya kamata shine dama yanada iyali? Fuskarsa kamar bata nuna ya kwana biyu ba, bama wannan ba irin lokutan da ya ware yake kiranta bata taba sannin cewa shi din mai iyali bane da bata ringa amsawa a lokuta irin wadannan ba, domin yana kiranta kafin a yi sahur fa, haka kuma bayan an fito daga sallar asham yana kiranta su dauki lokaci mai tsayi sunna magana, magidanci? A irin wannan lokacin ai ko yayane yana tare da iyalinsa, in ta yi duba da lokutan da Abanta yake gida kennan, sunna tare baki dayansu a gida fa? Ina laifin ya ware lokacin da yake kasuwa ? Sai ta ji wani iri, ama kuma maganar wai ko dan yanada iyali zata iya kasa amsa masa ko daya, to mem ake tunani ne? Ita dama abinda take tunani kennan da rayuwarta cewa lalle ba zata taba aurwn saurayi ba, to ita a haka din nan ta auri saurayi ta ce me ta yi kennan? Tap ai da kunyama wani abin , ita aurensa da ya'yansa saima tace adu'arta ALLAH ya amsa sai ta je su yi zamansu MUJAHEED ya dan sake muzgutawa ya ce" Hajia KAUSAR kar dai a saka na sare an min shiru?" KAUSAR ta sake sinne kanta ta boye fuskarta cike da nauyi da jin kunya ta ce" In sha Allah zan sanarwa su Mama, abinda suka yanke sai na sanar maka" Murmushi ya yi yana gyada kansa ya ce" Masha Allah, haka ake so, ya zamto ana tambayar amanar iyaye , to ama ke yaya kika ganni na maki ko?" Ta kofar hijab din take dan kallon nasa, yadda ya wani kanne ido sai ta ji kamar ta kwala kiran Mama dan ta zo ta tayata gannin wani makararan rashin da'a, ama kuma sai ta kwabi kanta ta sake sade kai har dai ya gaji da surutunsa shi kadai ya gaza samun yadda yake so ya hakura ya mike cike da mamakinta, kwarai ya yi mamakinta, domin halayarta sai suka so bambanta da wasu yanmatan da yake kulawa , yan matan da kamar jira suke a taya su? In ka je inda suke kuwa sai in Allah ne ya tsare maka amaninka, in ba haka ba tsaf za'a iya lalata da y'a a gidan iyayenta, ama ita tabarmar da ya zaunama bata hau ba kuma kanta da ta sada har ya mike ya ajiye alherin da ya ajiye wanda sam bata kula ba bata dago ba sai da ta ji yana yiwa su Mama salama ne sannan ta dan ciciba ta mike murya a fan sanyaye ta ce" A gaida gida da Y'ayana Elhaji, Allah ya hutar da gajiya" Yar dariya ya yi yana amsawa sannan ya sa kai bayan ya tabatar mata zai kireta fa kar ta kashe waya, ita kuma ta gama yanke hukuncin in sha Allah ba dai zata kuma amsa wayarsa a lokatan da take kyautata zaton magidanci na tare da iyalinsa, dan a yadda ta dafe din nan ta sha ruwan gidansu har ta batse ba zata so in ta zama matar aure a ringa yada mata mugwayen manufofi irin wadannan ba Fitarsa da amsa kiran TAUFEEK ta tabata ko mota bai karasa ba, ya sanar mata ta turo Aisha ta amshi sakon zasu fice, Da dan sauri ta ce" Aa, to bamu gaisa da ita ba zaka wuce ne? Bara na fito" Tana fada ne ta katse sannan ta karasa ta sanarwa Mama da dan sauri ta fita ta tsalaka ta karasa kusan motar gefen da yake dan dayan gefen da take bakin hanya ne ta mika hannunta suka gaisa tana fadin" Amaryarmu, kin kusa zama tamu dai yar uwa nan da yan kwanaki" Murmushi YUMNAH ta sakar mata tana fadin" Aunty Kausar har kin saka na ji kunya" Dan murmushin ya yi shima ya juya a zaunen da yake ya ce" Kin ga sakonki baya ni fa ba zan shiga gida ba dan so nake na kaita na wuce akoy aikin dake gabana mai yawa" KAUSAR ta je bayan ta bude motar tana fadin" Ba'a gama rikicin gidan bane TAUFEEK?, Ba zaka barwa HAJIA maganar ba" Da dan haushi kadan ya ce" Haka fa, HAJIA HAJIA tsohuwar nan ni da ita ne, ai ta gama siye ƴaƴanta tsaf sun ce sai dai na yi hakuri har ta amince min zaman gidana daban, KAUSAR ki je ki mata nasiha ta ringa jin tsoron Allah " KAUSAR ta kyakyace da dariya tana rike da marfin motar bata taba katon bokicin dake shake da tuyar da aka kawo masa ya sa Mamansa ta debar mata ba ta ce" Ni? Ai in na hadu da HAJIA ka tabata idasa ajiye maganar zamanka a gefenta zamu yi , TAUFEEK so kake dan shirin d amuke ya bare?" YUMNAH da zuciyarta ta cika da tambayoyi game da mutumen da ya fito daga gidan wanda sarai ta sanshi , sai kuma maganar da ake kamar ana nufin a cikin gidan nan za'a zaunar da ita ko menene? Ko dai itace bata fahimta daidai ba? Sai kawai ta ji wani abin TAUFEEK na fadin ta sauke bokicin mana ya sanar mata fa sauri yake yi? Hakan ya sa da sauri ta kalle shi ta kuma kalli baya tana zubawa bokicin ido cike da mamaki da wani tsoro tsoro dan bokicin ta tabata na gidansu ne daya daga cikin bokitan da aka yiwa TAUFEEK din ne na kwarya kwaryar sallah aka kai gidansu ai ? Da kyar ta sauke shi tana fadin" Menene a ciki?" TAUFEEK ya miko mata katuwar ambulop din katinta ya ce" KAUSAR daga wannan aikar kar ki kuma sakani wata kin fahimta?" Murmushi ta yi ta ce" An gama Yalabai, ama maganar dinkunnanka na wajen abashe ya yi kirana jiya baka leka ba ashe, sai kuma maganar wunin da muka yi da kai da kuma wankan ango da Mama tace a gidan su Uncle Abdallah za'a yi?" Yana yiwa motar ky ya kunna ya ce" Zamu yi waya idan na koma gida ki gaishe min da Mamanaa please " Hannu ta daga tana masu byby ta ce" YUMNAH na san sai ranar ko na kuma ganninki, sai mun je daukoki" YUMNAH dake hadiye wani makuku mai taurin tsiya da daci a wuyanta cike da takaici ta dan saki murmushin yake tana sake bin kofar gidan su Kausar din da kallo wanda a ranta take ayana ita ko kasheta za'a yi ba zata iya zaman minti daya a gidan nan ba , ama a cikinsa aka haifi rundumemiyar yarinyar nan da take neman hanna mata sukuni da kwonciyar hankali? Subahanalah wannan wace irin masifa ce? Sun koro da tafia cikin yannayi da dabara irin tamu ta mata ta ce" Sir, masha Allah gidan su Aunty Kausar ana samun baki, wanda ya fito ta yiwu uncle dinsu ne ko?" Yana tukinsa normal, a fuskarsa ba wani yannayi haka a yannayin motsin gabansa bayan ya tsayawa danja ya ce" Aa ba uncle dinta bane, Saurayinta ne Baki gane shi ba?" Cike da mamakin furucinsa da yannayinsa ta ce" Saurayi? Dama tanada saurayi?" Da dan mamakin yannayin tambayarta ya dubeta, sai kuma ya tayyar da motar ya bi ayarin motocin da suka yi gaba bayan danjar ta saki suka dauki hanyar gidansu dake kusa da wajen danjar Bai jima ba ya karasa kofar ya tsayar da motar a nutse ya kasheta sannan ya dan juyo ya zuba mata ido ƙadan Da kula sosai ya ce" YUMNAH na gode da ziyara" Murmushi ta yi tana dan sake kallon tsararen sajen fuskarsa da yannayin askin kansa mai fitar da fasalin fuska da tsarinta, sai kalar shadar jikinsa mai ruwan Ash color mai haske da ta dauki zare ashe mai duhu dinkin dan kadan ba wani da yawa ba A hankali ya dora da fadin" But daga yau, bana so kina fita, ko ina ne kin fahimta?" YUMNAH ta dan tsatsare fuskarsa da kallo, a hankali ta ce" Dama ba inda zan je Sir, sai wajen gyaran jiki kawai" Dan kureta ya yi da duban da ya sakata jin ta dan tsargu, sai kuma ya dauke kansa yana kallon gefe a hankali ya ce" ita mai gyaran ta zo gidan ta maki YUMNAH" YUMNAH ta dan zarro ido ta ce" idan gida ne fa akoy mugun tsada ne " Da mamaki ya dan mata kallon kai? Tsada? Shi zata kawowa maganar tsada? Tsada ta kai maganar mutuncinta da yake son fara karewa daga yau har karshen rayuwarsa? Tsadar me da zata kamo shi nashi kwonciyar hankalin? Baya tunanin in har zai iya hakuri shi TAUFEEK iyalinsa a waje da shigar da ba ita ba kowani shara na kallo da sunna ta tafi gyaran jiki A hankali ya ce" Kina iya fita" Fuskarsa ta tsatsare da ido, da dan sauri ta ce" Zan fa yi a gidan, ba zan tafi wajen gyaran ba" Motar ya kunna yana dan dage kafadunsa kadan , hakan ya sa ta kama marfin motar ta ce" Zamu yi waya da dare ne?" A hankali ya dan duba agogon hannunsa, ya tabata idan ya fito dare ya yi sosai, sai kawai ya dubeta da kula ya ce" Aa, ki yi kwonciyarki, zan kirayeki da safe in sha Allah" A hankali ta sake kureshi da duba, a zuciyarta kuwa tana ayyana ' Kennan ni ba zaka kirayeni ba dan zaka kirayeta?, Me sunnata ne wannan mata a duniyata ko nace a rayuwata?' Budewar ta yi ta fice ta shige cikin gidansu Tana nufar falonsu mesage na shigowa wayarta, sai ta ki dagawa tana sake kasa kunne dan gaskata idan har muryar yayarta ne 💔💔💔💔❤‍🩹❤‍🩹💔💔💔💔 *DA CIWO A ZUCIYATA* 💔💔💔💔❤‍🩹❤‍🩹💔💔💔💔 _MALLAKIN_ *SAJIDA NIJAR* *FREE BOOK NE* 🔟 LITATAFAN MARUBUCIYAR Duk karyar kada Yar mahaukaciya Neman na kaina Bani da zabi Bak'a ce Kutkale Makauniya ce Mage Duk nisan jifa Idan ka raina inda kake Dutse Alkalamin kadarata Bani da zabi Dakika Biyar Now *Da CIWO A ZUCIYATA* *Tallah, tallah, tallah* *SECRET DE LA FEMME DU MANGA* _Gidan Kamshi, Sirrin Manyan Mata, nesa tazo kusa,Amarya ,Uwar gida,Ango da mai gida Har ma da yan mata da samari shin kuna sane da cewa HAJIYA FUSAM ta shirya tsaf domin gwangwaje ku da turarakunta masu dankaran kamshi? Tare Kayan gyaram jiki na musamman ,wanda daga nesa kamshin ki kadai ya wadatar ya isar da sakon zuwanki waje,gidan ki kuwa sai ya zam abun kwatance wajen kamshi, kar na cika ku da surutu bara in fara zayyano su_ Farar Humura Bakar Humura Humura special, humura de bain Humura epicé Lait de nuit Parfums désodorisant Parfums rideau et dras Lait de nuit Alkam Kulakcam *Waɗannan kadan ne daga bangaren turaran ruwa* Gagab, sandal flex, Durot, durus, sandal fleur, tafarce, farce, sandal bangui, sandal, hypotonic sandal, al'ut, coktail creation VIP, Gajiji, Mankaji, turaran wutar labule da cafet, Aba malan, boulettes *Munada bangaren gyaran jiki kamar haka:* mai mai saka santsin jiki, mai mai kanshi, Kayan gyaran jiki mai saka fata ta yi santsi da laushi, kayan gyaran jiki mai saka fata ta yi fari, Sabulu mai saka fata ta yi haske, sabulu mai saka fata ta yi santsi, sabulu mai goge yanayin fata, mai wanda baya saka fari mai gyara fata Sayen na gari mai da kudi gida,sai an gwada akan san na kwarai💃💃 Hajiya Fusam na zaune a kasar Niger domin yin magana da ita kai tsaye tuntuɓi wannan number 97 82 44 94 *SECRET DE LA FEMME DU MANGA* Gidan Kamshi, Sirrin Manyan Mata💃💃💃💃💃 Da sauri ta daga kafarta ta idasa shiga tana bude sakon bankinta dake sanar mata shigowar makudan kudi na mamaki da ta tabata daga angonta ne, kuma kudin ba na komai bane sai na gyara Wa'inda in har gyaran zata yi ko amare ashirin ne ya ishe su tsaf harda suturun wunin biki da komai komai tsadar abin kuwa bale ita daya, sai dai maimakun ya mata dadi sai ta ji sam bata jin wani dadi ko zumudin abin har ta karasa ta zauna gefen yayarta dake wake ga amarya yar dangi ga amarya YUMNAH tana tafi da murmushi na farin ciki Yannayin YUMNAH ya sakata rage zumudinta tana kallonta sai kuma ta kalli mai aiki dake ajiye masu ruwa ta salameta ta ce" Ke lafiyarki kuwa ? Yannayinki ya nuna kina cikin wani bacin rai?" YUMNAH ta zubawa fuskar yayarta ido, a hankali hawayen dake makale mata suka samu damar zubowa , sai kuma ta fashe da kuka ta mike ta karasa ta fada jikin yayar tata , tana kukan sosai ta ce" Aunty, kun zo?, Sannunki da zuwa....." Hankalin yayarta a tashe ta dagota daga jikinta tana jan hijabin dake jikinta ta ce" Subahanalah ke kuka kuma? Menene? Subahanalah lafia? Me ya faru a gidan sirikan naki? Mama tace kin je masu barka da sallah har ina cewa me yasa kika fita yanzun fa kuma ba maganar fita in ba dole ba?" Tana kukan tana kallon auntyn nata, duda ta san yawancin lokuta yayar tasu ta kasance daban a yannayin halaya, domin wani lokacin harta da mamansu kwasa suke yi, bama a kan maganar saka hijab da sauransu in dai ta zo gari to fa sai an kwasa da ita kamar ba wace ke rayuwar turai ba haka zata ringa fadan a suturce jiki da sauransu dai abubuwa dai irin na tsauri Tana hawayen wani na korar wani ta ce" Aunty, TAUFEEK ne, Aunty lamarinsa ya fara damuna, abubuwan da nake gani sun fara tsoratar da ni, tun yanzu ina tsoron nan gaba ya zamo irin mazan nan masu kara aure, watau ya kasa hakuri da ni daya kwal a matsayin matar aurensa!" Kallonta take yi, bata katseta ba, tana kuma jira ta ji baban abinda ya sa kanwar tata ke kuka haka, dan kuwa ta tabata ba wannan kawai bane....domin in har wannan ne bata san me zata kirayi YUMNAH da shi ba, Sai dai ga mamakinta YUMNAH ta ja ta tsayar da maganarta tana ta shashekar kuka Fauziya ta ce" Ki daina kukan haka mana ki fada min menene wai damuwar? Dan na san ai ba zaki kasance mace mai irin ra'ayin nan ba, ko nace mai son sakawa kanta ciwo a banza da wofi ba, ina nufin yau mace komai kankantar shekarunta in dai ta fara amsa bayanan soyaya daga namiji in tana da hankali ai Auta ta san cewa ba'a halitoshi dominta ita kadai ba, bale kasancewarta musulma kuma y'ar hausa? Koda a gidanku ba'a yi ba kin gani a makota, menene zai dameki da irin tunanin nan tun yanzu salon ki kasa kula da kanki da maganar aurenki tun da jan sawunki a kan shirme? Ko kuwa maganarki da shi dama shi baya sonki kece ke sonsa zaki kai kanki inda za'a gaza hakuri da yarintarki a ringa maki uzuri? Ke Auta Allah na tuba ke da kika dauko dan kasuwa ai kin san ba dai a kan maganar mace zaki kawowa kanki damuwa ba ko????" Kukanta ba wani dainawa ta yi ba, saima ji da ta yi kamar damuwar ta karru a kan da Tana kallon yayarta ta ce" Aunty ba fa dan kasuwa kawai bane ba fa likita ne, kuma kin ga wata mata ce mai sunna KAUSAR wai take kawarsa ko me?, Aunty ya fi a irga zai amsa bukatun KAUSAR ni ya kawo nawa a matsayin na biyu, in karkare maki harta iyayensa sun santa kuma sunna zumunci da ita, bama kakarsa du masifar matar nan tana son KAUSAR din nan dan ni ganau ce ba jiyau ba , Aunty abin damuna yake yi fiye da tunaninki, ni da ace budurwarsa ce na rantse maki da na san yadda na yi da ita dan kuwa na fi karfin jagaliyancin ƴaƴan garin nan, damuwata kawai ita ba maganar soyayya tsakaninsu dan ai abin bama wani tsari in kin ganta ta yi hudunmu fa ni da ke, sa'arsa, kawai abinda yake damuna haushi take bani irin yadda mijin da zan aura yake bata lokaci fiyema da ni kaina, Aunty harfa kaya ake mana iri daya fa, ko kishiyata ce ai sai haka!" Kwarai, auntynta ta ji wani iri a bayanin kanwar tata, sai dai ko menene zata fi so a bishi a hankali, dan haka da kula ta ce" YUMNAH, mijinki yana sonki?" YUMNAH cike da bada tabaci ta ce" Kwarai kuwa yana so na" Auntynta ta ce" Shin a dan tsanin nan akoy wani abu da ya tauyeki da shi irin wanda aka saba tsakanin budurwa da saurayin da aka saka masu rana saboda ita? Ko kuwa akoy lokacin da kika fahimci ya so maki wata kyauta ta hanna?, Ina son sani ne dan na gane wani abin" YUMNAH ta yi gagawar girgiza kai ta ce" Aunty maganar kyauta ai ba za'a nunawa TAUFEEK ba, yana min harda ta mamaki dan kin ga allert din gyaran da ya sako min yanzu haka dan wai baya so na ringa zuwa wajen gyara, kuma gaskiya ban dai tsaya na gane ba a kanta dan ina iya cewa wani lokacin yakan kawon abu yace KAUSAR ce tace zai min kyau suka siyo min dai da sauransu...." Auntynta ta yi tsai tana hangen mamansu dake tsaye tana kallonsu ta baya ta harde hannayenta Dan murmushi ta yi ta ce" To shikenan, abinda nake so da ke Auta ki kula, kin ga a furucinki kan iyayensa kina sakin harshenki ya fadi abinda kika ga dama, ki kula Auta ki girmam masa dangi koda autar gidansu ne a haka shima zai girmama naki dangin, sai kuma maganar Kausar , ina so ki fadawa Allah, idan kin tashi fada ki barawa Allah zabi, ki sanarwa Allah in har damuwa ce a rayuwar aurenku ita din Allah ya maku tsari da ita, in kuwa alkhairi ce Allah ya haska zuciyarki a kanta ku yi mu'amala ta alkhairi, kin ga mijinki namiji ne tsayaye da yake da mutane a karkashinsa tun yanzu, baki fa isa ki hanna shi ire iren mu'amalar nan, bama kamar yanzu da zamani ya zo haka, wasun matan abokanan lalacewarsu nema, ba tsoron Allah ba tsoron ciwo ko kunyar ya'ya, kuma gasu ana zaune da su kalau har sun isa da gidansu, ki kula ki bi komai a hankali, yanzu ne zaki fara, kar ki yarda ki fara da garaje da shirme Auta, inama abin kukan da daga muryar da tayar da hankali a nan?, Kefa macece cikin salama sai ki yakicetaba ransa ta hanya mai kyau ba ta hanyar muzguna mata ba in har kin kula cewa alakarsu fa bayan zumuncin da wani abu a kasa, kin ga namiji kowa da halinsa, abinda suka yi taraya a kai daya ne lamarin mata, Auta in har kin yarda cewa ba ta wani waje kika gaza ba yannayi ne haka Allah ya halicesu sai ki ba kanki lafiya ki rayu lafiya a gidanki da walwalarki, in kuwa har baki yarda da haka ba ina tabatar maki wahala zaki sh........." "Ke, Auta bani wayarki " mahaifiyarsu da takaicin y'arta baba ya gama kamata ta karaso tana katse maganar da take yiwa kallon shirme ta amshi wayar y'ar tata ta duba adadin kudin da aka saka din na gyaran sannan ta mika mata ta ce" Tashi maza ki je dakinki ki yi wanka ki sha magani ki kwonta dan na san wannan kukan sai ya hadasa maki ciwon kai" Mikewa ta yi tana daukan hijabinta dake ajiye gefe ta juya ta shiga haurawa, dan har ga Allah itama maganar yayar tata ba wani birgeta take yi ba, maimakun ta tayata samo mafitar da za'a iya raba TAUFEEK da wannan karfen kafar sai ta wani shiga magangannu wasu iri, ai walahi bama zai yiwu ba, du yar shegiyar da zata duban mata miji sai inda karfinta ya kare, ba maganar boka ko malan magana ce ta kai da kai! Zama mamansu ta yi tana dauke kai hadi da hade fuska a lokacin da Fauziya murya a tausashe ta ce" Haba Mama, haba Mama, yanzu haka zaki nunawa YUMNAH bayan kin san maganar da nake fada mata gaskiyar kennan?" Rai bace mahaifiyarsu ta ce" Kim ga Fauziya dazu kika iso, bana son damuwa please, ba kuma na son mu fara raba hali, ke sai ki mance ni na haifeki ki ce zaki sakani a hanya , ki je kawai ki huta ki yiwa Mubaraka wanka na yiwa su Mahfuz, maganar nan kar ki saka kanki a ciki, ki barmin kawai na san yadda zan bilowa lamarin lokaci nake jira dan ba zai yiwu ba, mu da muke garin mu muka san wannan mu'amalar kuma muka hango ilarta, ko ciki daya suka fito gaskiya ba zamu iya yarda da kusancin nan ba tsar zamu raba bale wai kawa kawancen namiji da mace, irinsu ne ke hanna maka zaman auren kana ji kana gani , domin ko me mijinka zai kareka da shi sai sun amince" Ajiyar zuciya ta sauke, ba dan komai ba sai dan gannin maganar da alamu baba ce, kuma ba za'a barta ta shiga ba dan ra'ayi na iya bambanta, sai dai ta so su bata dama ta yi hanni irin na addinin musulunci ta kuma yi tuni da abinda aka sani, dan a ganninta yau macen da ta san ciwon kanta take kuma neman lahirarta zata yi domin Allah da kuma gyaran kanta, bayan wannan yaushe zaka saka damuwa a kan wanda aka halartawa irin hakan? Yau koda su biyu zai aura rana daya tanada abin fada ne? Wannan din kamar wata hanya ce da ta dauko wace ba zata bileta ko'ina ba, domin in har ta saka damuwar nan a ranta tabas ba zata rayu yadda take so ba, hakan na iya zama wata tawaya koma dalilin da zai ringa hadasa mata fitina da mijinta, bayan cewa namiji a waje da kuke saurayi da budurwa ne kake da damar ya tsaya ka tsaya in ta yiwu fine in ta bace kowa ya kama gabansa, daga bakin da ka zama malakinsa matarsa zaman zai cenza salo ne daga ka isa da shi zuwa ya isa da kai, watau rayuwa yar shawara yar samun matsaya mai kyau tare da yi masa biyaya, kai inma abinda ya shafi mata ne bama duka maza suke baka fuskar ka kawo masu maganar ba, tsaf za'a nuna maka ba huruminka bane kuma ka hakura kuwa ka zauna, domin wannan din ba cikakiyar hujar da zaka zo gidanku bane a kasarmu ta hausa Mikewa ta yi bayan ta yi fatan Allah ya sanyaya ta yi gaba kamar yadda Mamanta ta umarta Mahaifiyarsu kuwa ta dan girgiza kai cike da takaicin Y'ar tata ta fari, ita har mamaki take idan Fauziya na wani abin, kamar ba nononta ta sha ba , salo salo irin na ubanta, to ta je cen ta yi kanta ake ji ita dake zumunci kamar a hada kai da kishiya ita ta gano, na zata sakawa autarta sakaran ra'ayi tana zaune kalau ba A gidan su KAUSAR kuwa a lokacin da ta koma ta samu mahaifiyarta rike da kudin nan a zaune ta balbaleta da fadan a kan me zata bari ya bata makudan kudi har haka? To kuwa za'a mayar dan ba zata ja mata rigima da babansu ba, da kyar Maman nata ta yarda cewa bata san ya ajiye ba da bata yarda ba, haka suka yi jigum jigum har abansu ya dawo ya tarar da abinda ya faru, nan ya sake yin nasa fadan shima yace aaba za'a karba ba dan haka ta sanar masa idan ya dawo a bashi, baya cikin amsar kyautar mazan zamani ba'a san me gobe zata yi ba in Allah bai yi su din ne mazan ya'yan ba a zo ana rikicin kudin da bashi da su bashi da inda zai hako su, dama shi haka ya hori ya'yansa, bai cika son irin kaye kayen kyautar samarin nan ba, in ba an san da maganarka har ta yi karfi ba a fara amsar irin abu dan jefi jefi kyauta irin ta sallah da sauransu ba, to kuwa koda sun amsa ba da sanninsa ko na mamansu bane, Mahaifin nata ne ya ajiye da kansa da nufin in ya dawo a mayar masa da abinsa Washe gari kusan karfe goma da zai fita ya fitar da kudi masu yawa har kusan dubu talatin a cikin ajiyarsa ya ba mahaifiyarsu cewa ta ba KAUSAR ta samu wani abin da ta ga ya dace ta yiwa TAUFEEK kyauta na tayashi murnar aurensa, duda kadan ne ta kamanta , sannan suma zasu yiwa iyayensa daga bangarensu Sosai Mama ta yi farin cikin haka, kuma kwarai ta san hakan ya yi, domin ko rijiya tana son kari kuma ita kula dadi ne da ita , idan har suka kamanta ta tabata za'a ji dadin hakan domin iyayen na TAUFEEK masu karamci ne, sosai ta yiwa mijinta godiya da fatan alkhairi, ita ta san auren namiji mai zuciya ya fi wani mai kudin, domin mijinta Allah ya masa zuciyar nema da kuma sannin ya kamata, mutun mai matukar jajircewa a kan iyalansa, azumin nan aka yi aka gama bai taba fashin yawon kasuwa ba, kuma a kadan yana shigowa da ribar dubu takwas in kasuwa ta yi mugun dadi har sama da haka, in kuwa kasuwa ta cije wani sa'in har kasa da biyar, a haka yake cire yan bukatunsu na su yan fruits haka ko kifi haka sauran kuwa ya juye a asusun da ta tabata yanzu kam ya yi nauyi sosai, kuma a haka ya cire na hidimtawa yaron da yake hidimtawa y'arsa, lalle zata iya cewa ita kam ta dace duniya da kiyama tana fatan ƴaƴanta su samu mazaje masu fahimta da fita hakin iyali Bayan ya tafi ta samu su KAUSAR din a daki ta bata kudaden da suka sakata ihun murna da farin ciki, zuciyarta cike da kauna da tausayin mahaifinta, a duniya tana fatan Allah ya bata aikin da zata talafi mahaifinsu da mahaifiyarsu da shi, iyayenta sunne iyaye talakawa masu zuciyar fita hakin ya'yan da bata taba gani ba a duniya, tana sonsu tana tausaya masu tana taya su kula da tarbiyarta kuma ta yi alkawarin in sha Allah ba zata kasance daya daga cikin ya'yan dake jazawa iyayensu azabar ubangiji ta hanyar yada badala a doron kasa ba....nan fa suka shiga tunane tunane da neman abinda ya dace ta ba TAUFEEK matsayin gift, su ce wannan su ce wancen, har dai kansu ya kule suka rasa mafita, sun tsaya a tsakanin biyu, agogo ko Turare....sai dai shima sun fadi ne dan jin dadi dan kuwa ita ta san a turarukan TAUFEEK da wahala in yanada na kasa da dubu talatin , hakama agogon hannayensa bama zata iya kidaya kudinsu ba dan ta tabata masu tsadar gaske ne, maganar suka ajiye kan zasu bincika wajen kawayensu yan gayu su ji sunnayen turaruka sai su zabo na daidai kudin Wannan kennan ___________________________________ Kwana biyu tsakani KAUSAR da A'isha suka shirya suka je gidan aminiyar Aishan, dan ta nacewa yayarta cewa dan Allah ta zo su je dan matar ta iya mak'up tana so su dauki ranar da zata masu domin aure dai yau saura kwana takwas cif, anko dinsu kansu daya ne kawai basu amsa ba Da kyar suka samu gidan, domin ta jima rabonta da ita, sunna dai haduwa a school lokaci zuwa lokaci dan ita Usainar yanzu ta fi ba harkar kwaliyarta karfi babar mai harkar mak'up ce a garin Sun samu tarba ta mutunci, sun kuma taki Sa'a ranar hutunta ce bata kwaliya dan haka suka zauna suka shiga fira KAUSAR kam da hankali du ya dauku a irin sansanyan kanshin da falon matar ke yi na turaran wuta ta gaza hakuri ta ce" Kai Usaina ama dakin nan naki na kanshi mai dadi walahi, haka nake son kanshi mai sanyi da ratsa zuciya" Murmushi Usaina ta yi tana fadin" Lah aunty ki ce kanshin akoyshi har yanzu? Kin kuwa san tun jiya da dare da na turarawa dakin ban turara yau ba, sai da yama nake son turarawa, ai matar nan ta iya hada turare na kasa da kasa, haka na fesawar da kuma humurar akoy wace sai ta yi sati a jikin tufafi kanshin na nan radau, ai baban Abdul baya hanna kudi in dai turaran HAJIA FUSAM za'a siya" Aisha dake murmushin itama tana amsar wanda ta mikowa KAUSAR ta sinsina sai lumshe ido take yi itama ta sinsina ta ce" Kai, ama kawa wannan da tsada ko? Na san wannan in zaka shiga sia ka shirya" Usaina ta sake mikewa ta dauko mata turarukan ta ce" Ke kuw kawata, abu mai kyau ai shi ke siyar da kansa, tsada kuma ai karkon kennan, balema har ga Allah kayanta ba tsada, ga kyautatawa, kw harda gift take sako maka bayan na kudinka fa, kin ga wannan gift din ne , in takarkare maki kin ga dai baban abdul babban mutun ne ko? To walahi turaranta ne yake aiki da shi yanzu, cewa yake yi ko irin wunin office ya kama shi in ya je sake alwallah haka zai ji kanshin na tashi a ruwan, ke abokiyar zamana tun tana jin haushin hakan har ta hakura , nan fa yake amsar turaran wutar wai in zai kwana wajenta ya je da shi, ke dai har abu ya isheta ta nemi Hajia FUSAM itama ta shige, ni yanzu a gidan nan kin ga harta maina a wajenta nake siya da sabulu nawa da na yaranki, kin san kuwa ai kyau ya sa na nace" Itama Aisha yanzun dariya ta yi dole dan yadfa Usaina ta yi, sai take ji a zuciyarta kai dolema ta samu mu'amala da matar ko dan ta dan gyagyara masu harka, ah to magana ta kanshi da gyara wa ya ki? Bale ance da sauki ai kawai zata gwada sa'arta, tana shirin tambaytar numbar natar KAUSAR dake ta faman sinsinar na ruwan dake hannunta ta ce" Usaina kuma a ina take? Ina so, ni kam tunda kin ce harda na maza ina son na mazan" Usaina ta ce" Aunty yar Nijar ce ai, yanzu haka dai tana damagaran kuma ba inda bata aika sako, ga numbartama +227 97 82 44 94 , sunnanta kuwa shine HAJIA FUSAM" Numbar suka kwafa sunna jin farin cikin hakan, dan kuwa irin yadda turaran ke gyare a daure da wata fulawa mai kyau ta tabata a kanti ba zasu samu irinsa ba, dan kuwa hadawa ne take yi da tsararun nagartatun turarukanta su bata kanshi mai ma'ana da sace zuciya...., Sai daga baya nema suka tsayar da lokacin kwaliyar, ita da kanta ta ce su zo karfe goma ta masu kafin dai a dawo daga daurin aure in sha Allah Sun dan jima a gidanta kafin suke yi mata salama, Har sun kusa fita ta biyo su da sako leda baka ta mikawa KAUSAR tana murmushi ta ce" Aunty ga wannan, kin ga yannayin fatarmu kusan daya ce mu ba baki ba mu ba haske bau ba, ki ringa shafawa fuskar kafin ranar kwaliyar, na tabata sai kin siya da kanki a wajen hajia FUSAM" Godiya sukai mata sosai Wannan shine mafarin shirye shiryen auren TAUFEEK Tunda satin auren ya kama kuwa ya zamto babu mai lokacin kansa, duka bangaren biyu cikin shige da ficen shirye shirye suke, harta Kausar ba'a barta a baya ba domin bata zauna ba ta yi nan ta yi nan, ga wani abinda ya faranta mata rai 💔💔💔💔❤‍🩹❤‍🩹💔💔💔💔 *DA CIWO A ZUCIYATA* 💔💔💔💔❤‍🩹❤‍🩹💔💔💔💔 _MALLAKIN_ *SAJIDA NIJAR* *FREE BOOK NE* 1️⃣1️⃣ LITATAFAN MARUBUCIYAR Duk karyar kada Yar mahaukaciya Neman na kaina Bani da zabi Bak'a ce Kutkale Makauniya ce Mage Duk nisan jifa Idan ka raina inda kake Dutse Alkalamin kadarata Bani da zabi Dakika Biyar Now *Da CIWO A ZUCIYATA* *Tallah, tallah, tallah* *SECRET DE LA FEMME DU MANGA* _Gidan Kamshi, Sirrin Manyan Mata, nesa tazo kusa,Amarya ,Uwar gida,Ango da mai gida Har ma da yan mata da samari shin kuna sane da cewa HAJIYA FUSAM ta shirya tsaf domin gwangwaje ku da turarakunta masu dankaran kamshi? Tare Kayan gyaram jiki na musamman ,wanda daga nesa kamshin ki kadai ya wadatar ya isar da sakon zuwanki waje,gidan ki kuwa sai ya zam abun kwatance wajen kamshi, kar na cika ku da surutu bara in fara zayyano su_ Farar Humura Bakar Humura Humura special, humura de bain Humura epicé Lait de nuit Parfums désodorisant Parfums rideau et dras Lait de nuit Alkam Kulakcam *Waɗannan kadan ne daga bangaren turaran ruwa* Gagab, sandal flex, Durot, durus, sandal fleur, tafarce, farce, sandal bangui, sandal, hypotonic sandal, al'ut, coktail creation VIP, Gajiji, Mankaji, turaran wutar labule da cafet, Aba malan, boulettes *Munada bangaren gyaran jiki kamar haka:* mai mai saka santsin jiki, mai mai kanshi, Kayan gyaran jiki mai saka fata ta yi santsi da laushi, kayan gyaran jiki mai saka fata ta yi fari, Sabulu mai saka fata ta yi haske, sabulu mai saka fata ta yi santsi, sabulu mai goge yanayin fata, mai wanda baya saka fari mai gyara fata Sayen na gari mai da kudi gida,sai an gwada akan san na kwarai💃💃 Hajiya Fusam na zaune a kasar Niger domin yin magana da ita kai tsaye tuntuɓi wannan number 97 82 44 94 *SECRET DE LA FEMME DU MANGA* Gidan Kamshi, Sirrin Manyan Mata💃💃💃💃💃 Ga wani abinda ya faranta mata rai shine sakon kyautar da zata yiwa Taufeek, gefe guda kuwa Elhaji ya zo kuma ta mayar masa da kudin ama abin mamaki sai ya je ya duka da kansa gaban Mama yace da ita kudin nan ba rokarsa ta yi ba, haka kuma yana iya ba wanima a titi bale wace yake neman aure, da kyar Mama ta amshi kudin, shima dan ya bata kunya sosai irin yadda ya duka din, duda ta san ta girme shi sosai domin dan yanada mata da ya'ya ba wani baba bane, kawai kudi ne suka kwonta ya tara mata abinsa, su kuwa suke gasar haihuwa kamar yadda aka saba Ana gobe auren Mama da makociyarta suka je gidan suka kai gumbar da suka yi da nono da siga a cikin manya kwala shar shar shar da ledar goron HAJIA suka tare a bangaren Hajiar dan kuwa basu je direct wajen Mamansa ba, wajen Hajiar suka sauka makociyar Mama sai mamakin wai dama nan ne gidan su TAUFEEK take yi, domin irin yadda suke ganninsa bajaja a anguwarsu sun zata da kudin ama bai kai haka ba, saima da ta ga abin mamaki kyautar nan da suka zo da ita kamar sun kawo duniya guda, domin HAJIA haka take murna tana farin ciki ta saka yan aiki suka dauka ta ja su Maman suka nufi ciki wajen matan nan wani kallon yacewa makociyar Mama gyara kar ki kifa, ga abin gyare gyare na tarban baki da murnar babar rana, ga yannayin matan kowace da irin nata salo, sai katon falon ya bada kala babu wajen da ba abin kallon talaka ba A haka suka karasa sama wajen Mama suka wuce Hamdiya da bakuwarta ta sha kunshi da kitso kai kace itace amaryar dan a yau dinma dinkin dake jikinta an watsa da zinari ba kannanun kudo bane dan a yagawa kishiyoyi da bakinsu sai yadda hannu take tana karbar baki ta ko'ina dan sun yi gaya sosai ko dan su caji aljihun Elhaji wanda murnar wannan rana ta saka ya bude bakin aljihu fiye da da mikawa yake yi du abinda aka bukata ba kauron hannu Sosai Mama ta yi farin cikin gannin sakon nan, nan take ta saka aka ringa sakawa a frij tana fadin an taimaketa ba sai ta yi ba, ta kuwa manta da maganar dan faro faro mai sanyi na baki, haka take yiwa Mama godiya har sai da ta ji kunya ta lulubeta sannan ta rike su Mama aka shiga hada hada har dai dare ya yi kafin ta sake su tana faman maimaicin fadin" Maman KAUSAR dan Allah fa a zo da wuri goben, kuma ki cewa KAUSAR na ga ta zo yau, koda yake TAUFEEK yace dazu ya leka ya kai mata shadarsu ta diner kuma ya ajiyesu wajen kunshi, ni dai kii fada mata saura gobe ta yi zamanta sai ta ga an hantse na ganta a nan" Mama kam dariya take yi aka saka direba ya dawo da su gida da tarin alkhairi irin na girke girken gidan bikin da ake tata yi ana zubawa baki Bayan tafiyar su Mama, Maman TAUFEEK na cikin hidindimu kira ya sameta daga wajen mijinta Tana shiga ta same shi tsaye a falonsa na farko yannayin fuskarsa a hade tamkar wani abin ya bata masa rai Tun kafin ta zauna ya tareta da yannayi na bacin rai ya ce" Me nake ji haka a wajen yan uwanki ne Umin Boy?, Yaya zaki ki saka su a lamarin hidimar auren nan bayan sunna nan sunna kaf kaf da ransu sunna fatan birgeki? Me yasa komai sai dai ki tare ko dan ke kika haifi Elhaji karami ne?" Da mamaki ta kafe shi da ido, sai kuma ta sauke dubanta a kan matansa, sun sha kwaliya tamkar zasu je gasar kyau, kowace sai walwali take yi haka kuma fuskarsu a sake ainun da suka yi ifo hudu A hankali ta ja numfashi muryarta a raunane ta ce" Ka yi hakuri, ba za'a sake ba, in bandama abin iyayen Elhaji karami har sai an saka su abu nasu? Ni a sama nake ina fama da bakin da suka zo daga gida ai gidan baki daya a hannunsu yake, inace harta masu dafa abincin maza da aka dauko kannin hajia ne ko menene?" Wani irin makuku ya zo ya tokare wuyan Hajiar, har ga Allah ta tsani in ana kwatance a ringa nuna kanninta dan tuwo tuwo ne dan a habaicin da suke mata har nunawa ake yi kamar dan daudu, wani takaici ya kamata su da suka zo dan su saka yau ranar da ta fi kowace rana mahinmanci a duniyarta mijinta ya fatataketa ta yadda har a daura auren ba zata fahimci komai ba dan bacin rai su ga ta tsiya sai gashi dan bakin munafurci irin nata ta wani bashi hakuri tana sinne kai bakar munafuka Elhaji kuwa sai ya cire kai daga yannayinta ya ce" To a kiyaye, taron nan shine na farko a gidana kuma shine mafi daraja da zan gabatar dan auren yarona ne baba kuma namiji daya kwal, babu wace zan saurarawa idan ta dagan hankali ciki harda ke mahaifiyarsa, ku je ku bani waje dan baki ne da ni kuka kirayeni na zata wani abin ne mai mahimmanci, in sha Allah gobe daurin auren safe zamu yi ina son gama abinda ke gabana na zo na dan huta" Wannan shine bata lokaci bukata bata biya ba, a haka suka bar wajen nasa baki dayansu kowace ta nufi inda ta fi wayo, Mama kuwa ta ki nuna fushinta ta ci gaba fa hidindimunta sama da kasa domin su dakunnansu suka wuce , hakan ya sa ta rungumi abinta hankali kwonce ta ci gaba da hada hadarta da fatan du wani abu da suke nufi da ita ya kare masu dan ba zata biyewa fitintinnunsu a irin wannan babar ranar ba A lokacin da su Maman KAUSAR suka dawo gida nan suka baje ana ta raraba abincin ana mikawa makota sunna ta maida kirki da datako na wannan ahali, lalle abin ya ba makociyar Mama mamaki kuma irin yadda ta ringa maganar cewa take yi ai komaima sai a yiwa bayin Allan nan sun san darajar dan Adam........ Su Kausar kam kowace na nata uzurin ama kuma sunna jin firarakin su Maman har dare ya yi sosai ta mike ta shafa sabulun nan na wajen FUSAM ta barshi ya dan huta a fuskarta sannan ta wanke tana shafa fuskar ita da kanta cike da mamakin irin santsin da fatar nata ke yi, wannan dan fari farin na fatarta du ya fita yanzun sai wani sheki da fatar take yi ko bata shafa mai ba bata mata futu futun nan A nutse ta kwonta a wajenta zuciyarta cike da farin ciki da fatan gannin babar ranar amini, dan uwa, aboki, yaya a wajenta, lalle wannan rana tana daga daga cikin ranakun da take fatan gani a duniya na alkhairi, Murmushi ta yi tana dafe kitson da kai mata na hannu kora baya kannanu rass tana tunanin wai atach irin na kitson nan suka siyo rauda rauda za'a saka masu a keya, ita kam bata san ko zata iya yarda da wannan bidi'ar ba, sai kuma ta sake sakin murmushi a hankali ta furta" Gobe dai in sha Allah zan raka ka dakinka Besty, ina farin cikin hakan, Allah ya nuna mana ya da matarka ce har aljanna".... A'isha ta yi murmushi itama tana jin Adu'ar yayar tata, a hankali ta lumshe idannuwanta tana tunanin gobe, watau gobe idan da rai da lafia sai sun kafawa yayarsu tarihin da bata shirya ba, domin sai sun yi mata kwaliyar da bata taba yi a fuskarta ba, har fata take yi safia ta yi a yi ta ga yaya fuskar zata dawo, har aunawa take yi a zuciyarta shin yaya kwaliyar zata amshi yayarsu? Ta tabata wanda baya kwaliya idan ya yi yana yin kyau, to ama ita yayar tasu zata amince ne?.....haka dai kowa da irin zumudin dake zuciyarsa suka yi barcinsu sunna dan tsinkayo firar mahaifinsu dake ta murnar an yi murnar kyautarsu duda ba wani taka kara ta yi ta karya ba.............. Da safe kusan karfe tara Aba ya fice a gidan da nufin wucewa wajen daurin auren direct, Mama kuwa ta gama kimtsawa ama jira take yan matanta su gama hada kayansu su fita tare ita zata je da yan anguwa ne su kuwa zasu wuce wajen kwaliya ne Karfe tara da minti arba'in da yan kai suka sauka a gidan Usaina da akwatin kayansu madaidaiciya mai dauke da suturun da zasu cenza suka ajiye kayan sunna kallon yadda dakin kwaliyar nata ya kawatu masha Allah kamar ba a kasar hausa ba, har sai da KAUSAR ta ji tana sha'awar malakar dakin kwaliya Rukaya ce aka fara dandasawa kwaliyar, KAUSAR na kallo tana jin anya zata iya kuwa wannan hoda haka? Ana tsaka da yin kwaliyar ta lalubo wayarta gannin karfe goma ta gota sosai ta shiga gwada neman layin TAUFEEK tana tunanin zuwa yanzu ai ta yiwu har sun dawo gida dan karfe tara ne daurin auren Kiran farko ba'a daga ba, sai a na biyu ne aka daga Muryarsa a hankali, cike da kamala ya furta" Asalamu alaiki wa rahamatullah" Cike da murmushi ta furta" Wa iyaka, Sanar min abin farin ciki Ango....." A hankali ya yi dan murmushi yana dan tare hularsa da abokinsa amininsa kuma bakonsa ke son ja dan tsokana , ya ce" KAUSAR...." KAUSAR ta yi dan tsai jin muryar nasa wata iri, a hankali ta ce" Lafiyarka kuwa? Ko kukan angwaye ka yi da aka daura?" Murmushi ne ya subuce masa jin abinda ta fada, sai kuma muryar abokin nasa na fadin" Bani ita, KAUSAR yaya aka yi kika yi wannan rashin kirkin kika ki zuwa ki rakamu wajen daurin auren bestynki? Bestyn kennan? Gayanan yana ta kuka muna rike shi wai ango ne shi" Yar dariya ce ta subuce mata tana zarro ido ta ce" Lah, ka zo? Na shiga ukuna yau da tsokana, ai ganinan na fi so in ya dawo na wuni inai masa nasiha sannan da ni za'a rakashi dakinsa danma kar ku cutar min shi" Kasancewar sun saba dama, idan sun hadu ko a waya ne sai sun yi ta tsokanar junna sunaiwa junna neman rigima mai ban dariya shi yace shine bestyn TAUFEEK, ita tace yaushema ai shima ya sani ya kauce ya bata waje bata son rigima dai da sauransu , hakan ce yanzunma , tana ta murmushi ta ce" Gaskiya ni ka bashi wayar sai nake jinsa kamar a takure, me ka masa ne dan bana nan?" TAUFEEK dake kallon titi direba na tuka su shi da Alhhusain ya yi murmurshi ya sake zubawa hanyar ido har suka karaso yana jin rikicin amininsa da aminiyarsa ya amshe wayar a tausashe ya ce" Ki tabata na ganki in ba haka ba ina iya yin fushi KAUSAR" Zata bashi amsa ya katse kiran yana kallon kiran YUMNAH dake shigowa Murmushi ya yi ya ki dagawa saboda sun karaso gida ne ana ta busa ana hayaniya kala kala idan yace zai daga ba zata ji shi ba sai ya soke wayar a aljihun rigarsa ta ciki a nutse ya ringa shiga jama'a murmushi kwonce a saman fuskarsa yana cikin shiga irin ta danyan yadi mai laushin gaske, wanda laushinsa ne zai nuna maka karkonsa da kudinsa a ido, mai dan duhun haske ama ya dauki zubi madaidaici a babar rigar, sai hula nutsatsiya mai yannayi da suturar jikinsa Daria take yi bayan ta kashe ta yi ido hudu da Aisha Haba ta dafe ta ce" Wannan abin na idannuwanki bakya ji ya maki rumf A'isha? Innalilahi wannan ni a titi ai ba zan shedaki ba, uw awara jarumar indian film dai wannan hanci an sake janshi haka?" Aisha ta saki murmushi itama ta ce" Aunty saura ke taso ki ga a maki mu tafi kar a cinye miyar kari fa" Kausar ta mike tana cire katon hijabinta ta karasa tana sake kallon kitson yadda aka boye shi a bayan daurin dan kwalin kamar ba kari ba, sai dai yadda ya malalu ai mai hankali dai ya san ba gashin bahaushe bane Tana kallon Usaina dake hada kalolin hoda dan ta fitar da kalar fuskarta ta ce" Ama Usaina ni ba zaki saka min abin karin ba ko? Ni dai gaskiya kin ga wannan katon ribom din nake so nawa yake shi? Ni karin gashin nan sam bana so" Usaina ta yi murmushi ta ce" Aunty, tsaya mu gama sai mu ga in ribom din zaki fi jin dadi a jikinki sai a saka shi, shima ai yanada girma sosai kuma kasa kasaa muke saka shi sai dauri ya hau kansa ya zauna, ama shi daurin da ake masa simple ne irin na zahrah buhari dai haka" Ita dai sarautar Allah ta zubawa ido aka ringa juya fuskarta nan a juyo nan, ama ta ki a saka mata abin saman ido mai kalolin nan, sai dai sun ci karfimta gashin ido sai da suka saka mata madaidaici daidai da yannayin fuskarta, haka kuma jan bakin Nude ne aka saka mata ba mai karfi bane kuma ba'a yi mata barbada kumatu ba, kwaliyarta dai simple ce, kwalin nema ya so tsayar da su domin da kyar idon ya daina hawaye aka diga mata abin wanke cikin ido idon ya yi haske sosai sannan ta mike ta dauki nata lesh din itama ta zagaya baya dan sakawa domin sai ta saka za'a daura mata dan kwali Hankali tashe ta yaye labulen dake karewa ta ce" 💔💔💔💔❤‍🩹❤‍🩹💔💔💔💔 *DA CIWO A ZUCIYATA* 💔💔💔💔❤‍🩹❤‍🩹💔💔💔💔 _MALLAKIN_ *SAJIDA NIJAR* *FREE BOOK NE* 1️⃣2️⃣ LITATAFAN MARUBUCIYAR Duk karyar kada Yar mahaukaciya Neman na kaina Bani da zabi Bak'a ce Kutkale Makauniya ce Mage Duk nisan jifa Idan ka raina inda kake Dutse Alkalamin kadarata Bani da zabi Dakika Biyar Now *Da CIWO A ZUCIYATA* *Tallah, tallah, tallah* *SECRET DE LA FEMME DU MANGA* _Gidan Kamshi, Sirrin Manyan Mata, nesa tazo kusa,Amarya ,Uwar gida,Ango da mai gida Har ma da yan mata da samari shin kuna sane da cewa HAJIYA FUSAM ta shirya tsaf domin gwangwaje ku da turarakunta masu dankaran kamshi? Tare Kayan gyaram jiki na musamman ,wanda daga nesa kamshin ki kadai ya wadatar ya isar da sakon zuwanki waje,gidan ki kuwa sai ya zam abun kwatance wajen kamshi, kar na cika ku da surutu bara in fara zayyano su_ Farar Humura Bakar Humura Humura special, humura de bain Humura epicé Lait de nuit Parfums désodorisant Parfums rideau et dras Lait de nuit Alkam Kulakcam *Waɗannan kadan ne daga bangaren turaran ruwa* Gagab, sandal flex, Durot, durus, sandal fleur, tafarce, farce, sandal bangui, sandal, hypotonic sandal, al'ut, coktail creation VIP, Gajiji, Mankaji, turaran wutar labule da cafet, Aba malan, boulettes *Munada bangaren gyaran jiki kamar haka:* mai mai saka santsin jiki, mai mai kanshi, Kayan gyaran jiki mai saka fata ta yi santsi da laushi, kayan gyaran jiki mai saka fata ta yi fari, Sabulu mai saka fata ta yi haske, sabulu mai saka fata ta yi santsi, sabulu mai goge yanayin fata, mai wanda baya saka fari mai gyara fata Sayen na gari mai da kudi gida,sai an gwada akan san na kwarai💃💃 Hajiya Fusam na zaune a kasar Niger domin yin magana da ita kai tsaye tuntuɓi wannan number 97 82 44 94 *SECRET DE LA FEMME DU MANGA* Gidan Kamshi, Sirrin Manyan Mata💃💃💃💃💃 Hankali tashe ta yaye labulen dake kare mai saka kaya ta fito tana fadin" A'isha wannan rigar fa? Ji fa yadda ta min daga nan?" Ta fadi nan din tana nuna wajen cinyoyinta irin yadda rigar ta dameta ta fitar da yannayin kirar jikinta Ido da baki da hanci Usaina ta saki tana mamakin Kausar, kai subahanalah, da haka yannayin jikinta yake take fama da zumbulelen hijab kamar zata kifa? Haka yannayinta yake yanzunma ta zo da wata riga ne bubu zumbuleliya wace bata kama ko'ina na jikinta ba sai yawo take a ciki ashe ashe abinda ke kasa kennan? Su sunna yiwa Aisha kallon masha Allah mai manyan mazauna ashe ga wace tace kau bani waje, eh lalle Kausar tanada tumbi wanda da ace bayanta ba pankameme bane haka da tsaf zai iya zamewa matsala a kwaliyarta, sai dai yanzun haka kadan ne ake ganninsa sakamakon yannayin halitar da Allah ya yi mata, sosai suka taimaka suka rufe mata yannayin tumbinta saima su da suke bugon idannuwa Nan fa aka shiga rikici, domin firr ta ja ta tsaya kan ba zata saka rigar nan ba, sai dai bata sani ba tsiya ce kannen nata suka shirya mata domin kaf kayan lesh din shine dama dama wanda ya dan rufe mata sutura Tamkar zata yi kuka haka take sake maimaicin ba inda zata iya fita a haka, ba zata iya ba Gannin rikicin na gaske ne Usaina ta je ta dauko wata alkyabarta baka mai shara shara, shara shara ne da ita sosai alkyabar dan yan mata ke yawan sakata sai yan gayun matan aure , itama irin shigarta kennan , Alkhyabar ba wani abu da take boyewa sai dai ta dan kare dai , sunna ne domin gwarama mayafi da ita , nan ta dawo tana budewa ta ce" Aunty, kin ga wannan alkyabar sabuwa ce sau daya tak na sakata in har zaki iya sakawa mu gama daurin ki saka ki ga zata rufe fa" Kausar dake zaune ta harde hannu ta gama kutuntumawa Aisha da rukaya ashar sai huci take kan bafa zasu fitar da ita tsirara ba jiki a sanyaye ta ce" Usaina ni da a je a daukon sabon hijabina na sallah da muka yi sai na rufa, yaya zna rabaki da kayanki kumaa bayan wannan nauyi da muka dora maki?" Usainar ta ce" Lah, aunty walahi ba wani maganar nauyi, kuma ba maganar aro tsakaninmu, kin ganta in dai zaki saka din ni zan ji dadi, yanzu yaushe aka koma aka dauko maki hijab aka dawo inace yanzu Mama ta gama fadan baku karaso ba?" Shiru ta yi, du nauyi ya damu zuciyarta, haka aka daura mata daurin da ya idasa fitar da sirrin kwaliyar sannan ta saka alkyabar wace ita da kanta sai ta tsaya gaban madubin a hankali tana shafa yan kannanun walwalin gaban alkyabar farare karkar ba masu yawa ba tana gannin yadda alkyabar ta hau yannayin dinkin har kasa da irin yadda kwaliyar ta hau kalar fatarta tamkar ba ita ba A hankali ta daga idannuwanta ta kalli kannenta da suka sakata a tsakiya sunna kallon madubin su dukansu Wani ni'imtacen murmushi ne ya kwace mata a fuskarta a hankali ta ce" tabarikalah masha Allah" Aisha ta saki murmushin itama a hankali ta ce" Tsarki ya tabaka ga ubangijin da ya halici samai da kasai da dukan halitun ciki, Aunty kwaliya tana maki kyau sosai haka dama?" Rukaya ta yi murmushi itama a hankali ta ce" Tamkar ba aunty ba, kalli yadda ta yi? Inama Elhaji ya ga kwaliyar nan na tabata yau zai ce a daura aurenku" Da yar dariya ta mintsini hannun Rukaya sannan suka juyo Usaina ta ringa kashe masu hotunna sunna faman fadin ta ajiye masu zasu zo su amsa a wanke a fitar masu tunda babu mai babar waya a cikinsu Sai bayan sha biyu na rana suka fito daga gidan kwaliyar suka shiga adaidaita wace Rukaya da kyar ta samu waje dan wajen matse masu yake sai sun jijirga suk dauki hanyar gidan su TAUFEEK da akwatinsu Sunna karasawa suka tarar gidan dinke da al'uma, babu kalar da babu tun daga tsofafi har zuwa yara kannana, kai yan matan dake gidan tamkar gida mai yan mata bayan yan matan gidan basu wani girma ba, yan matan cikin gidan ne dangi ne da ango dinsu na safe, sai dai ba irin lesh din su KAUSAR ba domin wannan su Mama ne suka yi shi iri guda sai makusantanta da ta ba ita da kanta, lesh ne mai daraja da tsadar gaske hakan ya sa har suka karasa bangaren Maman akan bisu da kallo ne ga tsararen kwaliyarsu ga lesh din jikinsu sai a yi tunanin wasu makusanta ne wa Hajia watau mahaifiyar TAUFEEK din yinin biki kawai ake yi ba ji ba gani, biki irin na manya masu hannu da shunni Kokarin dukawa take yi dan gaisar da Mama da ta nufota tana murmushi hakoran makarta biyu na walwali ta saka hannayenta ta tareta tana fadin" Oyoyo yarinyata, koda yake fada ya dace na rufe ki da shi, ama ba yanzu ba sai mun salami baki zan maki tass a gidan nan, zo maza ga abincin TAUFEEK dauki yana bangaren Hajia dan Allah kai masa ki dawo ku je da yan uwanki bangaren cen na amarya ku kai na baki ance zasu iso su yi gyaran dakinta dan yau za'a kawota" Baban faranti mai dauke da kula biyu masu marfin kwalba rantsarsu ne Mama ta saka aka miko mata, a dan gagauce Maman ke bayanin dan yannayin taron kuma dama zata fita ne ta samu wanda ta yarda da shi ya kaiwa TAUFEEK abincin sai ga KAUSAR din, hakan ya sa ta juya da abincin su kuwa su A'isha suka bi bayan Maman domin ta ja su ne tana fadin" Ku zo ku kuwa yayana kafin ta dawo a shirya na bakin, ga mamanku cen a dakina da baki idan mun gama kwa gaisa" A nutse take nufar hanyar bangaren Hajiar har ta karasa ta saka kafarta a hankali ta bude tana ta Adu'ar Allah ya kaita lafia domin takalmin kansa da take kai da kyar take rike kanta a sama, ga alkyaba ga kuma kwaliyar da take jin kunya kamar me wace tana ji a jikinta da wahala ta iya wuni da wannan hodar a fuskarta da sauransu A hankali ta saka kanta falon tana yin salama Jin salama ya saka Hajia dakatawa wace ke shirin shiga kicin sai fada take yi tana yadda hannun anma rainata a kan me za'a bar mata jika da yinwa har sha biyu? Lalle zata iya sabawa uwar ɗan nan, shine fa zata shiga ta ga abinda zata sama masa koda danwake ne kafin a jima a bashi tuwo sai ta ji salama Da farko furkar ta zubawa ido, sai kuma ta shiga binta tun daga kanta har zuwa inda ya fi tsole mata ido da sakata zarro ido kamar zasu fado kasa Da sauri ta yi ribasss ta juyo ta karasa shigowa ta zo inda TAUFEEK kw zaune da Alhhusain sunna dan zantawa ta zauna daf da shi hadi da riko hannunsa na hagu ta jimko da bakinta ta shiga nuna masa abinda take ganni yau ra'ayne da ayne Alhhusain ne ya amsa salamar a bayane sosai yana juyowa, sai kuma shima ya dan zarro ido kadan dan har ga Allah da farko bai gane fuskar ba da yannayin har sai da ta saki murmushi tana idasa shigowa gaba dayanta ta nufo falon bayan ta cire takalman ta ce" Ka ga abokin ango, menene nake gannin ka yi wani laushi ko yinwar ne kaima?" Hajia ta saki hannun TAUFEEK da ya irin cire kan nan ya ki kula KAUSAR ko kallonta bai yi ba shi kam wai fushi yake yi sai yanzu zata zo aurensa dan wulakanci, ta tafa hannayenta tana tare gefen kuncinta ta hade da dan kunnen zinarin dake kunnenta ta ce" Na ga annabi in na yi hali na gari, yar nan Ke ce? Dama haka kike ama kike lumbukewa a hijabi bakya ko shafa fankeke? Lah ha ila ha ilalahu muhamadu rasululahi sallalahu alaihi Wa salam ku duba ku ga halitar ALLAH a yanke masha Allah kamar kamar lah kamar mema zan ce ke ama kina kokari haka kike tafia ras irin nawa.......?" KAUSAR wani irin tsuru tsuru ta yi tana kallon Hajia, TAUFEEK ya zubawa hajia ido kafin ya juyo da dubansa dan gannin meye wai ya saka hajia magana haka?, Alhhusain kuwa sai ya mike ya amshi farantin dan yadda ta yi sai ya so bashi dariya ta yi tsuru tsuru kar ta saki abincinsu , shi da kansa mamaki ya kasa barinsa haka kuma idannuwansa sunna matukar son kare mata kallo duda ya san hakan kamar ai ba daidai bane kau? Ido ya zuba mata, fuskarta ita ta fi bashi mamaki, kwaliyar dake zane a saman fuskar nata ta fi bashi mamaki, sai dai bai san cewa abin mamakin a gaba ba sai da ya dan so gannin meye yankawar da Hajia ke fada ya dan kalli yannayin shigar jikinta a dan gurguje ba da nufin komai ba sai dan ya ga wani hijab ne ta saka wai HAJIA ke wannan surutun sai ya ga wani ikon Allahn da ya so sakashi kyatsa rantsuwar sam bamaa ita bace ta hanyar dauke kansa da sauri ya juyo barin hajia , sai dai yanna kallon Hajiar ya ga ta tsatsareshi da ido da duba wani kala daban irin marar kyau din nan kuma da ido tana aniyar neman yin tsegumi da shi bayan cin naman wani haramun ne dan haka ya kauce idannuwansa ya hade fuska sannan ya mike tsaye daga zaunen da yake ya daga kafarsa zai karasa sai ya ji hannunsa rike taf a na hajia, Dubanta ya yi sannan ya kalli hannun nasa ya ce" Sakeni mana" Sai a lokacin Hajia ta saki hannun tana sakin harare ta ringa lekawa ta ga ya karasa inda KAUSAR ke tsaye ya mata nuni da ta wuce ciki, sumui sumui ta yi cikin ta tsaya shi kuwa ya karasa ya tsaya gabanta da sauri yana hade fuska ya bude baki zai yi magana ya ga HAJIA ta masu tsuru tsuru sai zarro ido take yi hakan ya sa ya sake jin wani takaici ya lulube shi ya ce" Hajia meye wai?" Hajia ta tabe baki ta ce " Meye kuwa, miya ce, me zaka fada mata ne?" Ikon Allah....., Ya ayyana a zuciyarsa ya zamto sunna kallon kallo su ukun Yannayinta da sanyi ta ce" Ka yi hakuri besty gidan kwaliya muka tsaya shi yasa fa bamu karaso da wuri ba, ka tambayima su Aisha " Da bacin rai ya ce" Haka fa, gama katt na gani, yanzu meye anfanin haka KAUSAR? Kefa ba wata yarinya bace da zaki biyewa yara ki je ki yi wannan abin ki biyo titi, yanzu ko kunya bakya ji???" "Yo kunyar uban wa kake so ta ji ? Yau ga jaraba auren wani shegen ke kanta da za'a hannata yafe ta zaga gari? Da yafen nan take na rantse da huwa rahamanu ɗan nan na tabata da yanzu y'ar nan ta yada na biyar ko na shida ta dauki wani cikin dan bana tunanin akoy shahashan da zai iya hakura da y'ar nan,kuma nice nan makaryaciyarka zaka ga yadda zata yi kasuwa, dama abinda ke hijabin nan kennan???" Hajia ta fada, hankali kwonce har tana dafe haba Gaba daya wata irin kunya ce ta nemi halaka KAUSAR A tsayen da take sai ta duke tana rufe fuskarta a cinyoyinta ta furta" innalilahi HAJIA, na shiga uku aa fa" TAUFEEK dake tsaye ya rasa wanene ya dace ya yiwa wa'azin jin tsoron Allah a tsakanin Hajia da ita wannan yarinyar da ta tashi tana rufarta a kamilance ta wani saki jiki kamar ba KAUSAR ba? Kai wannan abu ya bakanta masa rai menene wannan shashancin? Rai bace ya juya, har ya nufi falon ya dawo ya nunota da yatsa ya ce" kin ga daga falon nan in kafarki ta fita waje sai na saba maki KAUSAR, ba zan kyaleki da mutuncinki ki ringa yawo haka ba, shirme kawai kin iya sakani gaba ki wankeni in na dan yi wani abin kamar wata ta Allah kece ke yawo haka, an ji kunya!" Ya idasa fada ya yi gaba Hajia dake rike da haba al'ajabi na neman sakata marmaren yan maye na iya shegen Elhaji karami ta duko ta gyara daurinta ta nuno KAUSAR da yatsa ta ce" ki ji ni da kyau , ni nan nice uwar uban elhaji karami, kin ga kuwa na ga duniya gannin idona, nice zan fada maki mai fisheki, in bamu maki aure ba kwadaki zamu yi mu cinye ne? Kin ga kwaliyarki ba rashin kunya ko rashin kamun kai a ciki, Allah na tuba yo alherin nan ai ba kowa ke samu ba, tashi maza kada su baza su ki shige jama'a babu abinda za'a yi, in banda bakin hali irin na Elhaji karami in aka hannaki kwaliyar kika rasa mijin shi zai ji dadi ne! Ana abu ba tsoron Allah sam? Tashi maza wataya bikin amini kike shagali maki gani ya mutu dan bantan uba !" To fa, Hajia kin kuwa zo da tsoron Allah anya?😁😁😁😁😁😁 Hajiar shagali 💔💔💔💔❤‍🩹❤‍🩹💔💔💔💔 *DA CIWO A ZUCIYATA* 💔💔💔💔❤‍🩹❤‍🩹💔💔💔💔 _MALLAKIN_ *SAJIDA NIJAR* *FREE BOOK NE* 1️⃣3️⃣ LITATAFAN MARUBUCIYAR Duk karyar kada Yar mahaukaciya Neman na kaina Bani da zabi Bak'a ce Kutkale Makauniya ce Mage Duk nisan jifa Idan ka raina inda kake Dutse Alkalamin kadarata Bani da zabi Dakika Biyar Now *Da CIWO A ZUCIYATA* *Tallah, tallah, tallah* *SECRET DE LA FEMME DU MANGA* _Gidan Kamshi, Sirrin Manyan Mata, nesa tazo kusa,Amarya ,Uwar gida,Ango da mai gida Har ma da yan mata da samari shin kuna sane da cewa HAJIYA FUSAM ta shirya tsaf domin gwangwaje ku da turarakunta masu dankaran kamshi? Tare Kayan gyaram jiki na musamman ,wanda daga nesa kamshin ki kadai ya wadatar ya isar da sakon zuwanki waje,gidan ki kuwa sai ya zam abun kwatance wajen kamshi, kar na cika ku da surutu bara in fara zayyano su_ Farar Humura Bakar Humura Humura special, humura de bain Humura epicé Lait de nuit Parfums désodorisant Parfums rideau et dras Lait de nuit Alkam Kulakcam *Waɗannan kadan ne daga bangaren turaran ruwa* Gagab, sandal flex, Durot, durus, sandal fleur, tafarce, farce, sandal bangui, sandal, hypotonic sandal, al'ut, coktail creation VIP, Gajiji, Mankaji, turaran wutar labule da cafet, Aba malan, boulettes *Munada bangaren gyaran jiki kamar haka:* mai mai saka santsin jiki, mai mai kanshi, Kayan gyaran jiki mai saka fata ta yi santsi da laushi, kayan gyaran jiki mai saka fata ta yi fari, Sabulu mai saka fata ta yi haske, sabulu mai saka fata ta yi santsi, sabulu mai goge yanayin fata, mai wanda baya saka fari mai gyara fata Sayen na gari mai da kudi gida,sai an gwada akan san na kwarai💃💃 Hajiya Fusam na zaune a kasar Niger domin yin magana da ita kai tsaye tuntuɓi wannan number 97 82 44 94 *SECRET DE LA FEMME DU MANGA* Gidan Kamshi, Sirrin Manyan Mata💃💃💃💃💃 Dawowarsa da hijab din hajia na sallah rike a hannunsa ya saka hajiar yin shiru da bakinta daga hudubar da take yiwa KAUSAR ta zuba ido tana kallonsa Fuska a daure ya ajiye mata hijab din gefenta, murya cen ciki ya ce" I'm hungry,,,," Daga haka ya juya ya koma wajen zamansa fuskar nan tasa zaka rantse wani mugun abu akai masa Kausar ta saka hijab din bayan ta dubi yannayin hajia , a hankali ta zame dan kwalin dake ciki ta cire sannan ta iya mikewa tana jin wani nauyi na kwaliyar a ranta ta sake dakatawa tana dyban HAJIA Hajia ta hade hannayenta wajen kirjinta kasa kasa ta ce" Je zuba masa abincin sai mu dinke a daka na gama baki shawara, kin san dama shi magidanci tuwonma sai an zuba masa, matarsa dai zata ga iya shege, jibi keya uwa mun aikata sabo irin yadda yake harararmu, je zuba masa sai mu gama maganar " Ajiyar zuciya ta sake saukewa a hankali ta karasa inda suke zaune, Salisu na magana, Adamu na dariya yana duba abinda yake nuna masa, shi kuwa TAUFEEK din yana zaune ne yana kallon shima abinda suke yiwa dariyar wanda sam shi bai ga wani abin dariya a nan ba, wasu yan mata ne a tiktok ke tikr rawa tamkar zasu karya kaffafuwa sai kace wasu jakai, shine suka ga abin birgewa a nan Plate ta karo a kicin din HAJIA ta zo cikin nutsuwa ta zauna ta bude abincin ta shiga zubawa a zuciyarta tana ta tunanin abinda ta masa da yake jin haushinta, bata san ta inda zata kamo ba, batama san takamaiman laifinta ba, ta yiwu dan ta fito ba hijab ne, bai san itama fin karfinta su Aisha suka yi ba, da bata fito din a haka ba, lalle tana tausayawa YUMNAH, koda yake ta yiwu kuma in dai mai saukin kai da jin magana ce ba zata wahala a wajen mijin nata mai tsatsauran ra'ayi ba A hankali ta dago dubanta dan tana ji yadda abokanansa ke fira da raha,ama shi ya wani kyale su sunna ta zuba su kadai bayan gayar nan idan tana tune tasa ce Da idannuwanta ta bi inda ya zubawa ido, wato hannayenta dake rike da cokali mai dan girma tana zuba abincin, Wa'inda suke dauke da jan kunshi irin na yan mata da aka yi kata itama ta cancana abinta A hankali ta sake zuba idannuwanta a saman fuskarsa, hakan ya sa suka yi ido hudu da shi Bata saba dan sun yi ido hudu da TAUFEEK, TAUFEEK din abokinta ta fauke dubanta ba, ko yanzu da suke kallon ido cikin ido sai bata janye nata ba bale shi da take fadin kulun bashi da kunyar kallon idon mutun ya janye A saman labanta ta iya budawa kadan, kasa kasa sosai ta ce" Me yake damunka ne?, Fushin me kake yi? Wate ya bata maka rai?" Har ta ajiye maganarta yana kallon yannayin da ta yin, bai bata amsa ba ya janye dubansa a kanta ya maida wajen abokansa dake tataunawa sunna ta sako shi a ciki daga shi har ita Tana gama zubawa ta so zama, sai dai da ido TAUFEEK ya mata alamun ta tafi, hakan ya saka ta shaka, shaka irin ta jin haushi harma ta gaza hakura ta sauke masa duba mai shige da harara kasa kasa sai dai a kausashe ta ce" Malan in nice baka son gani a taron naka na yi tafiyata mana? Me na maka tunda na zo kake bina da kallo irin na tsana?, In wani ya taba ka ka huce a kansa mana sai mu dake tare da kai kuma a rana baba irin wannan? Karma ka kula nin TAUFEEK sai me?" Tana gama fada ta yi gaba da tafia irin ta sauro mai bayanar da irin tata baiwar wace ba kowa keda ita ba ama kuma idon kowa na iya ganni Wani takaicin ya sake shaka har ya saka hannunsa ya talabe habarsa dan takaici da rashin madafa Abincin sama sama ya iya cinsa dan ya riga ya gama fice masa a rai da abubuwan dake faruwa da shi a yau din Sai da suka gama suka fice da abokansa wajen da taron ya fi yawa yana ji kamar kansa zai buga dan ciwo, domin hayaniyar tana nema ne ta fi karfin kwakwaluwarsa Kusan karfe hudu na yama a dole ya mike ya shiga cikin gidansu dan irin hayaniyar dake ta tashi sama sama Ikon Allah ta tsaya yake kallo a lokacin da ya ga iyalan mai kwanoni sunna raba hali tamkar an aiko su, fada ne ko mema zai kirayi abin? Shi dai ya ga abin tamkar ba na masu hankali ba kuma kunnayensa na nema su sanar masa wace ake son takalowa Idannuwansa ne suka sauka a kan Maman su KHAUSAR dake tsaye da waren takalmi a hannunta , takalmin da ya san mamalakinsa , watau mahaifiyarsa Wanzuwarsa a wajen ya saka yawanci kame bakinsu suka yi shiru, domin TAUFEEK bako yake a inda yake so a ganshi bako, sanane shi a hali na dabanci da jagaliya idan halin hakan ya kama, TAUFEEK mutun ne mai hali kala uku a rayuwa, a gaban tsagera shi din baban tsagera ne, a gaban iyayensa yana da ladabi da biyaya da kishinsu, sai mace daya tak dake taka shi ta masa rashin kunya son ranta, ita kuwa baya fatan a wayi gari ta ga kalarsa da yan gari suka sani, ya fi so ya ci gaba da kasancewa mutun mai matukar laushi, sanyi, rashin sannin ciwon kai a gabanta, dan tana da daraja da mahinmancin da baya so idan ta gane waye shi ta tsorata da shi, Hular dake kansa ya cire a hankali yana sake bin yayar hajia da wani kallo mai kama da daf yake da budar bakinsa ya yi mata barin mahaukaciya komai girmanta da tsufanta kuwa, domin abu daya ne ta taka take fada daga bakinta wanda a duniyar nan baya tunani wuta ko mashi zasu hanna shi farautar mai zaginta, watau mahaifiyarsa, shi fa komai girmanka ka girmama iyayensa to fa zaka more shi fiye da tunaninka, idn kuwa ka yarda, ka kuskure, wata motsarariyar giyarka ta saka ka take masa martabar masu martaba babu abinda zai hanna shi aikata aiki irin na yaren da basu da tarbiya ta hanya watsa hannayens aa fuskarka ya ce da kai UWAKA ko kuwa ya ja baya ya shige ka kowa ya mutu a huta Da sauri hajia ta kama hannun yar uwarta tana fadin" Wai menene kuka tsaya kunna kallon mutane ba zaku iya raba fada bane jama'a? Dan Allah kowa ya kama gabansa tunda abin hakane, yaya zaku taru kunna kallon abu na faruwa ama kowa ya ja ya hade hannunsa ya nade yana kallo? Wannan ai sam bai dace ba" Da mamaki yar uwar tata ta kalleta jin furucinta, kasancewarta ita ta izata sosai kan su zo a yita ta kare kuma sai ta ji magana irin haka? Zata yi magana ta ga kula da abinda bata kula da shi ba da farko, watau TAUFEEK tsaye ya jinginu da abin labule idannuwan nan nasa sun kade sun yi jajir tamkar wanda ke shirin hadiye dan mutun yana bin kowa da kallo Bata iya yin maganar ba sai hannunta da ta warce ta shiga haurawa cike da takaici Hajiya Fatahiya ta saki yar guda tana sake yafa gyalenta ta ce" Wai rashin kunyar karya, ki ci gaba mana mu gani buge ko zobe zai ci nasara" Hajia Nawarah da abin mayarwar ama ta yi shiru ta bari zata rama ne, saima kokarin korar mutanen da aka tara na arziki ta shiga yi tana fadin tunda hakane kowa ya watse ai an ci an sha sauran sa yi A hankali ya dago daga inda ya jinginar ya nufo inda HAJIA Nawarah ke tsaye Gaban Maman KHAUSAR kuwa sai da ya kwonci kwonci ya fadi, a dan firgice ta zuba masa ido tana tunanin abin yi, domin mahaifiyarsa ne ta sakata zuwa dan kar ta bari ya aikata wani abin a wajen nan in dai ya ji hayaniyar da ake yi Har ya kusa cin mata da sauri Mama ta yi raf da hannunsa na dama tana cicira ido , muryarta a raunane ta ce" Aya D'an nan ina zaka je ne haka?" Dakatawar da ya yi, niyarsa ya warci hannunsa da karfin da zai saka wanda ya rike masa watsuwa a kasa, sai dai muryar da ya ji ya saka shi sake ambaton Allah, sannan a hankali ya juyo yana dan kakaro murmushi ya ce" Mama, hajia ce zan cewa kar ta kori kowa, a ci gaba fa biki kawai" Kai Mama ta gyada da sauri ta ce" To to to, ai ina iya fada mata ka je kawai abinka zan sanar mata in sha Allah " Hannun nasa da ta rike ya sake kallo, a hankali ya sauke yar ajiyar zuciya sannan ya yi gaba bayan ta sakar masa hannun Yana tafia Maman ta sake sauke ajiyar zuciya tana ta Adu'a a ranta sannan ta samu ta shiga bada hakurin laifin da bata san waye ta aikata ba Tsaki Hajia Nawarah ta ja sannan ta haye ta nufi dakinta Tana shiga ta tarda yayarta sai masifa take yi kamar zata tashi sama Zama ta yi saman kujera tana kallon yayar tata da ta ce" a kan me zaki hanna ni magana dan wannnan ya shigo? Bakima son bata bikin nan na ga alama, in ba shi ba kina ji kina ganni a ringa tafka maki wulakanci dan ana auren dan so? Ke baki haihu bane ko shegu kika haifa? Da ki bari na fada na ci uwar babar tasa idan ya so na ga abinda ya is aya yi, in shine karshen marar kunyar duniya ya rama mata" Murmushi mai ciwo Nawarah ta yi tana cire rigarta dan wanka zara shiga domin ta gama hada gumi ta ce" Ba zaki gane ba, ko a haka mun cakulata domin mutun ce da bata son hayaniya, sgi yasa bata cika zama a falo bama , wai ita y'ar gayu bata son hayaniya, na tabata tana cen tana hawaye, abinda ya sa na hanna ki magana na rantse maki da wanda raina ke hannunsa yana iya zabga maki mari a kan uwarsa, kuma babu abinda za'a yi, ke in fada maki aunty saima abin ya kare a kanmu domin yana iya hannaki shigowa gidansa a kan d'ansa, dan ko ya masa fada na bai kyauta ba ya mari mai shekaru to fa zai dawo ya min wanda ya dame nasa ya shanye, abinda na so uwar ta biye min mu hadu mu lakada mata dukan tsiya, sai wannan banzar yar kazagin nata ta jata ta haudata ciki, kuma ta dawo ta dauke takalminta daya da ta yar, na so koda takalmin ne mu samu mu ba kawar nan taki dake fadin a kawo takalminta a ga aiki da cikawa, Aunty da ace inda hurumin kashewa ko rayawa matar cen bayan na kashetama sai na koneta kurmus, domin ta tare min gaba ta tare min baya, na rasa abu da yawa sanadiyarta, ana min kallon Hajiar mai kwanoni ni ba kowa bace idan tana waje, a dai je sha'ani kawai, ama na yiwa kaina alkawari ko ba dade ko ba jima sai na ga bayan matar cen!" Jikinsa da tarin nauyi ya fice a falon yana sake dane abinda yake ji a cen kasan zuciyarsa A lokacin da ya zo shiga bangaren Hajiarsa, watau kakarsa ya ja yaa tsaya dole sakamakon gannin kanwarsa tsaye ta kafe shi da ido tana hawaye Fuskarta ya sake kafewa da ido abubuwa da yawa na ratsa kwonyarsa, ciki harda wani abu mai kama da kamar ya ji haushinta, wanda ya tabata ba komai ne ya janyo masa jin haka ba sai wulakancin da mahaifiyarta ta gama bazawa yanzu a cikin falon cen Da sauri ya cire kansa yana Adu'ar neman tsari da shedan , yawancin lokuta yakan rasa me yasa idan ya tsinci kansa a irin haka sai ya ji kamar zai ji haushin ƴaƴansu kansu bama su ba, bai san yaya zai yi kwatancen ya dace a ringa kiyaye ido idan za'a yi halaya na wulakanci wa mahaifiyarsa, sai dai ba komai ya san ya zame masa wajibi ya yi biyaya ya kuma bada example wa kannensa kamar yadda mahaifinsa yake fada a kulun Hannunta da ta rike nasa tana kukan ta ce" Yayanmu, dan Allah ka masu magana su daina, ka ga fa ba abinda aka yi suka kama wannan rigimar, me yasa suke mana haka ne?" Fuskarta ya dan sake kafewa da ido, sai kuma ya budo bakinsa zai yi magana Kiran da ya shigo a karamar wayarsa baka ta aikin sirrinsa wace idan kira ya same shi irin haka to urgent ne ya saka shi da dan gagawa fadin" Ki daina kukan nan, ki wuce bangarenku ki yi wanka ki yi alwallah lokacin sallar magarib ya kusa, bana son ki shiga abinda ba'a saka ki ba kin fahimta?" Baima iya gane amsarta ba ya shiga falon na hajia da dan sauri ya dauki ky din motarsa ya fice *Tallah2* *ALLAH BAI SAUKAR DA CIWO BA SAI DA YA SAUKAR DA MAGANINSA* Ni ce dai Fareeda Abdallah, na sake dawo muku da tallen magungunanmu da zuwa yanzu bazan iya ƙayyade yawan waɗanda suka dace da biyan buƙata sanadiyyar amfani da maganinmu ba. Alhamdulillah! Ƴar'uwa ki gwada, wataƙila warakarki na tattare da maganinmu. Haihuwa ce baki taɓa yi ba ko kuwa jinkiri kike samu sanadiyyar planning ko kuma haka kawai? Muna da ingantaccen maganin rashin haihuwa ga mace da namiji, wanda za ki bada sadakar 2k ga matsalar ko wane ɓangare. In sha Allah za ki dawo da godiyarki bayan amfani da maganinmu. Sanyi (infection) ne yayi miki yawa yake saka ki ciwon mara, zubar farin ruwa, ƙaiƙayi, ƙuraje, ɗauke ni'ima, har ma ya saka mijinki ya dinga miki gani-gani saboda bakya gamsar da shi? Da naira 3k zamu haɗa miki magungunan da za kisha ke da Oga in dai kika yi amfani da su ku da sanyi har abada in Allah ya yarda. Muna sayar da ingantaccen haɗin sabaya, wanda zai sa nonuwanki su cicciko, hatta fatar jikinki sai ta murje sanadiyyar shan kunun sabayarmu. 2500 bokiti 1litter. Muna da maganin wankin nono ga mai ciki da mai shayarwa, wanda indai kikai amfani da shi yaronki zaiyi tubarakallah, ba ruwanki da laulayi. Muna da ingantaccen maganin Daji (Cancer), typhoid, maleria, yaron da yayi nauyin ƙafa, da sauran cututtukan da ban ambata ba. Muna aika maganinmu ko ina tsakanin Nijar da Nigeria, ga masu buƙatar magani da gaske su tuntuɓeni akan lambar wayata 07039080978, ko 09077591726 Noted: *MAI SON MAGANINMU IDAN BA A KADUNA YAKE BA, SHI ZAI YI KUDIN MOTARSA HAR ZUWA INDA YAKE, BABU INDA BAMA TURAWA IN SHA ALLAH.....SAI KUN ZO* ......................m💓💓💓💓💓 💔💔💔💔❤‍🩹❤‍🩹💔💔💔💔 *DA CIWO A ZUCIYATA* 💔💔💔💔❤‍🩹❤‍🩹💔💔💔💔 _MALLAKIN_ *SAJIDA NIJAR* *FREE BOOK NE* 1️⃣4️⃣ LITATAFAN MARUBUCIYAR Duk karyar kada Yar mahaukaciya Neman na kaina Bani da zabi Bak'a ce Kutkale Makauniya ce Mage Duk nisan jifa Idan ka raina inda kake Dutse Alkalamin kadarata Bani da zabi Dakika Biyar Now *Da CIWO A ZUCIYATA* *Tallah, tallah, tallah* *SECRET DE LA FEMME DU MANGA* _Gidan Kamshi, Sirrin Manyan Mata, nesa tazo kusa,Amarya ,Uwar gida,Ango da mai gida Har ma da yan mata da samari shin kuna sane da cewa HAJIYA FUSAM ta shirya tsaf domin gwangwaje ku da turarakunta masu dankaran kamshi? Tare Kayan gyaram jiki na musamman ,wanda daga nesa kamshin ki kadai ya wadatar ya isar da sakon zuwanki waje,gidan ki kuwa sai ya zam abun kwatance wajen kamshi, kar na cika ku da surutu bara in fara zayyano su_ Farar Humura Bakar Humura Humura special, humura de bain Humura epicé Lait de nuit Parfums désodorisant Parfums rideau et dras Lait de nuit Alkam Kulakcam *Waɗannan kadan ne daga bangaren turaran ruwa* Gagab, sandal flex, Durot, durus, sandal fleur, tafarce, farce, sandal bangui, sandal, hypotonic sandal, al'ut, coktail creation VIP, Gajiji, Mankaji, turaran wutar labule da cafet, Aba malan, boulettes *Munada bangaren gyaran jiki kamar haka:* mai mai saka santsin jiki, mai mai kanshi, Kayan gyaran jiki mai saka fata ta yi santsi da laushi, kayan gyaran jiki mai saka fata ta yi fari, Sabulu mai saka fata ta yi haske, sabulu mai saka fata ta yi santsi, sabulu mai goge yanayin fata, mai wanda baya saka fari mai gyara fata Sayen na gari mai da kudi gida,sai an gwada akan san na kwarai💃💃 Hajiya Fusam na zaune a kasar Niger domin yin magana da ita kai tsaye tuntuɓi wannan number 97 82 44 94 *SECRET DE LA FEMME DU MANGA* Gidan Kamshi, Sirrin Manyan Mata💃💃💃💃💃 A haka sallar magariba ta shigo , harma isha'i ta shigo, ya zamto masu haramar daukan amarya har sun shirya sun tafi , ciki harda mahaifiyar su KAUSAR, Kausar din kuwa kacokam a bangaren Hajia suka wuni da yan uwanta , harma ta je amsowa hajiar maganin ciwon kai sai dai wanda ta siyo din ba shi hajiar ke so ba, hakan ya sa Hajia saka hijabinta ta sakota gaba cewar bara su koma tare tunda gidan ba mutane sosai kuma tana son mike kafarta itama ta yiwu zaman waje dayan da ta yi yau ne ya hadasa mata ciwon kan A hankali suke tafe, wajen siyar da maganin ba wani nisa da gidan, layi na biyu ne kawai kemis din mai maganin yake Maganin KAUSAR ta kalla a karro na ba adadi ta ce" Hajia, maganin da kike son mu amso fa bai dace kina shansa yanzu ba, kin ga da kin sha zai rabaki da ciwon ne na dan lokaci, ba'a son shan ire iren magungunnan nan, ni kam da wannan din kika sha ya fi wancen anfani" Hajia ta dan kalleta shekeke ta dauke kai ta ce" Ke kuwa, ko kece Magidanci kya shafa min lafiya, shima sai iya yin tsiya idan bani da lafia na je asibitinsa ya kama min iya yi kennan, shi yasa na samu mai kemis din nan ya zama abokin sirrina, ya zamto idan dai bani da lafia to yana gefe zai bani magani na hadiya an gama, ba sai na je wajen Magidanci an sosoke ni da allurai ba ana min iya yi" Murmushi kawai KAUSAR ta yi tana tunanin to magidantan na Hajia har nawa ne? Ita dai daya ta san tana cewa Magidanci TAUFEEK, kennan ba shi kadai bane take fadawa hakan?, Abinda dai ta sani shine ba TAUFEEK bane Hajiar ke nufi, domin TAUFEEK dai TAUFEEK karatunma ai bana ne suka gama tare da shi Dale su da hasken mota ta yi ya saka su ja suka tsaya Da sauri Hajia ta riko hannun KAUSAR kasa kasa tana fadin" Ke mu juya kar a sace mu Y'ar nan" KAUSAR din kanta haske sun ya dan tsorata ta, dan yanzu yannayin insecurity din da ake fama da shi dole idan ka ga wani abin ka kiyaye Bude motar aka yi aka fito, a kusan tare suka sauke ajiyar zuciya gannin TAUFEEK ne da abokinsa, sai dai kafin ya karaso inda suke tsaye wata motar ta zo ta makunma tasu daga baya har sai da motar ta yi gaba kadan sannan ta tsaya Da sauri ya juyo ya zubawa wanda ya karrun masun ido, da kuma abokinsa da ya nufi wajen a fusace yana dauko wani ashar irin na an bata makan nan ya lailayawa wanda ya zo da a kori kurarsa ya bugun masun bayan ba wani a kan hanya suka tsaya ba Juyowa ya yi yana kallon yadda Hajia ta makalkale masa hannu jikinta na rawa tana zarro ido ta ce" Nu kam kamar wace ban yi addu'ar fitowa ba?mene wannan din kuma" A hankali ya dauke dubansa daga kanta ya sake dorawa kan Kausar dake tsaye fuskarta a cure waje waje daya alamun har yanzu fushin take yi da shi , kuma yanzunma wani hijab ne da yake iya kiransa a tsokali adini domin sam ba irin hijab din da ta saba sakawa mai rufe suturarta bane , ta wani kebe baki uwa an mata laifi A nutse ya ce" Ku kuma daga ina kuke da daren nan?" KAUSAR zata bashi amsa, Hajia ta rafka wani irin salati da karfi tana dafe fuskarta tamkar ita ce aka wankawa mari ta ce" Aan kafta masa mari, an kaftawa abokinka mari, ka ga ya yi kashangar kar aje ya summa, kamo shi mu tafi gida mema ya hada shi biyewa mutumen da ya tardo mota ajiye ya make? Ai da gani a maken yake shima" Da mamaki ya sake zuba idannuwansa, ai kuwa abokinsa ne dai abokinsa Adahir da ya hadu da shi yanzun a asibiti ya biyo da shi dan gidansu bayan layi ne motarsa ta samu matsala aka shekawa marin da ya saka shi zama ya dafe kuncin ya shiga tunanin rayuwa da abubuwan al'ajabinta, daga zuwa jin ba'asin an yiwa motar makocinsa barna ya samu hannun kato a gefen haba har yana jin bakon yawu a bakinsa ga dukan alamu an sabauta masa matauna Hannunsa ya janye ya karasa wajen bayan da hannunsa na hagu ya masu alamun su juya gida , ya karasa wajen da har ya fara daukan tsirarkun mutane yan taya bera bari ana ta kokarin rike mutumen da shine ya zo ya yi barnar ama sai warce hannu yake yana fadin a barshi ya sabautawa Adahir fuska in yana takamar shi mai kudi ne shi ba abinda ya shafe shi da kudinsa , gidan horon hali ne ba yau ya saba shiga ba A tausashe ya ce" Soubahannalh" bayan ya yi ido hudu da Adahir dake tsugune uwa an girgiza bera a kwano, ya cire dubansa yana saukewa kan Mutaka mai Shago ya ce" Soubahannalh, ku sake shi mana me ya yi zafi haka ne malan?, Ko dai a hanya ne muka tsayar da motar ne ni ban gane ba" Hannunsa ya warce rai bace ya ce" a hanya ne mana, in ba a hanya ba a gidan uwar mutun ne?, Zaku zo ku ajiye mota a hanya dan an karu ba'a gani ba ku zagi mutane, idan rama masa ka zo yi ai sai ka matso in kai namiji ne na ci uban baba............" Cikin ikon Allah sauran zagin da ya dibo daga bakinsa yake tunanin ya gama amayarwa dai hadiye shi ya yi a zuciyarsa a lokacin da gefen fuskarsa ya amshi naushi irin na kato dan uwansa , Naushin da yake tunanin da katon itace ne aka mauza masa shi, sai dai idannuwansa suka sheda masa mutum ne ya yiwa fuskarsa shima barin mahaukaciyar da ya gaza tantance zuwanda da sauke masa shi a fuskar Ihu ya sake , lokaci daya ya kama hannun Mutaka mai shago da yale salalamin gannin abinda bai taba ganni ba MAGIDANCI na fada , da karfi ya warce hannun ya janye Mutakan ya durfafi wanda ya buga masu mota idannuwansa na rintsewa ya kamo wuyan rigarsa ya hade da makogwaronsa ya rike da riko irin na gaskiya da gaskiyar nan sannan ya aniya jijiga shi a tsayen da suke kafin ya sake shi kasa Da sauri ya shiga nade hannayen rigarsa, sai dai gannin kamar zasu tsayar da shi mutane na kokarin hannawa ya saka shi dauke rigar gaba daya ya cire daga jikinsa ya yi ciki da wannan mai akori kura da ya shiga hali na dana sani da tunanin inama hannun agogo zai koma baya da sun zanta sun sulhunta kansu cikin salama ba tare da hankalin kowa ya tashi ba Da gudu KAUSAR ta sakarwa Hajia maganinta a lokacin da Hajia ta fashe da kuka hannaye saman kai tana ihun a raba fadan cen jikanta ne Magidanci ne kuma yau yake ango kar a zane shi ko a raunata mata shi ta rasa tudun dafawa, a lokacin ne ita kuma KAUSAR ta karasa muryarta na rawa , jikinta na rawa ta duka ta dauki rigarsa da yar karamar wayarsa da ya yar a nan dan masifar dake cin zuciyarsa wadda yake neman wajen amayarwa wunin yau cirrr bai samu ba sai yanzu a rikice ta ce" Freind, Freind, innalilahi wa inna ilaihi raj'une, Bawan Allah ka hanna shi mana wayo Allahna" Lokaci daya ta fada tana riko hannun Atahir da ya samu kansa gannin su ke cin wasan ya mike yana aukin fadan ci ubansa kar ka barshi Docter ci UBANSA ta rike tana dan jijigawa dan ya bata hankalinsa Da kyar su Mutaka suka kwaci mai akori kura da hancinsa ke zubar da jinni har ya bata gaban rigar TAUFEEK dan matse masa kai ya yi a hamata ya rike taf ta yadda zai ji jiki ko bai summa ba ya yi kannin sumar, danma hamatar ba hamami ai da ya garda rana ya kuma shanye hanyar a kansa kamar sunnansa Kamar ana tura mota baya haka suka masa suka samu ya yi baya sannan aka shiga bashi baki, ciki harda daidaikun datawan anguwan da suka sanshi suka kuma san wannan din ba halinsa bane tabo shi aka yi, kuma abin ya mugun masa zafi har yau aka ga Magidanci da haka, Shi da kansa sai ya samu kansa da jin matsananciyar kunya, dan a cikin mutanen harda abokan mutuncin mahaifinsa da datawa masu daraja Maimaitawa yake ba komai , ba komai har ya karaso kusa da motarsa inda Hajia ke tsaye sai sharbar kuka take yi su KAUSAR na kusa da ita har yanzu KAUSAR rike tsaf da hannun Atahir hawaye na bin gefen kumatunta tana bin TAUFEEK da kallo tamkar bakonta A hankali ya dan shafa sumar kansa yana dauke dubansa daga fuskar Kausar ya karasa inda suke tsaye ya tausasa muryarsa ainun da nufin sake basu umarnin su shiga motar ya mayar da su gida idannuwansa suka sauka a hannunta rike da na Attahir shi kuma zuru zuru kamar sabon kamu sai kallon TAUFEEK din suke su duka Takaici ya nemi sake shaka, haushi haushi ya nemi kume shi, bai san lokacin da ya saka hannunsa ya raba hannayen nasu ba sannan ya jaa hannunta kiiii ya bude motar da hannunsa ya mata alamun ta shiga fuskarsa tamkar hadarin gabas Da sauri ta shiga tana matsawa tana sake zubawa fuskarsa ido Hajiama ta zo ta shiga tana rungume maganinta hadi da hannayenta a kirji ta yi tsuru tana hangensa sunna magana da Attahir Ajiyar zuciya Hajia ta sauke kasa kasa ta ce" Ko dai aljannu suka shafe shi yau?" KAUSAR ta mayar da bayanta jikin motar a hankali ta jinginar tana lumshe idannuwanta zuciyarta na ci gaba da dokawa cike da tsoron abubuwan da suka faru yau, dan a yau ta ga abubuwa da yawa da suka wahalar da ita ciki harfa fadan nan na TAUFEEK Bata sanshi da haka ba Bata san yana iya yin fada haka ba Tsoron da ta ji a lokacin da mai akori kurar ke zage zage ta kusan summa, dan tsoron da ya kama zuciyarta kar ya daki TAUFEEK din A hankali ta share hawayenta tana sake lafewa har ya shigo ya tada motar ya ja bai masu magana ba ya nufi gidan da su Sunna karasawa maimakun ya shige ciki kamar yadda kofar ke bude motocin daukan amarya sun dawo sai bai shiga da motar ba ya bude ya fita haka da farar singiletin dake jikinsa ya nufi wajen mai gadi dake tsaye da wasu mutane biyu Zurru Hajia ta kuma yi tana kallon sabon badala a wajen magidanci, ita sai ta rantse da huwa rahamanu yau gaba daya kamar an cenza mata jika, ku ga fa damatsuna a fili yana tafe a wajen da kila wa kala yana iya hadewa da sirikansa tunda an kawo masa mata yau, tana murnar bayan dogon lokaci dogon jira, dogon cece kuce da saka ido daga mutane daban daban yau Allah ya yi jikanta ya wanku sai gashi yana dambe? Dan jim kadan bayan mai gadi ya shige ciki shi kuma ya dawo bangaren da Hajia take Bude wajen ya yi a hankali ya zuba mata ido kamar yadda take kallonsa Murmushi ya kakaro kasa kasa ya ce" Wai kallon fa?" Hajia ta cire idannuwanta ta dubi gabanta , sai kuma ta dawo da dubanta kasa kasa ta ce" Ka tabata baka hadu da shafar aljannu ba yau?" Murmushi ya yi mata a bayane, sai kuma ya dan leka inda Kausar take zaune, a hankali ya ce" Ki bani rigar kar su Mama su tardoni a haka Freind" "Au wato mune ka rainawa wayo magidanci? Yanzu ace da girmanka ka tsaya dambe da jiki a fili? Kai fa likita ne, likitanma baba , sai ka bata lafiyarka ta hanyar gwada gwonji ?" Hajia ta fada tana janyo rigar tasa ta mika masa, sai dai bata janyo da wayar tasa ba, shima sam a wannan lokacin ya sha'afa da du wani tunanin waya har ya saka rigar ya gyara da kyau sannan ya fadawa Hajia ta fito zai kai su Maman gida ne dare ya yi Ta so ta nuna to ama shi ango yanzun kuma wani yawo zai shiga? Sai dai tunawa da ta yi waye zai kai gidan sai ta kame bakinta ta fito tana mika masa maganin da fadin ya cenzo mata ba zata yi asarar kudinta ba Yana tsayen har su Mama suka fito Kasancewar da aminiyar Maman su Kausar din aka wuni gidan bikin a dole Kausar ta fito daga bayan ta shiga gaba su kuwa su hudu suka shige baya Mama sai aukin fadin take da ya barsu su shige adaidaita ai kar ya wahalar da kansa, shi kuwa bai ce komai ba saima wani dan murmushi da yake saki fuskarsa na fitar da annuri da kuma wani girma na daban tamkar ba Taufeek dinta ba....................... *ALLAH BAI SAUKAR DA CIWO BA SAI DA YA SAUKAR DA MAGANINSA* Ni ce dai Fareeda Abdallah, na sake dawo muku da tallen magungunanmu da zuwa yanzu bazan iya ƙayyade yawan waɗanda suka dace da biyan buƙata sanadiyyar amfani da maganinmu ba. Alhamdulillah! Ƴar'uwa ki gwada, wataƙila warakarki na tattare da maganinmu. Haihuwa ce baki taɓa yi ba ko kuwa jinkiri kike samu sanadiyyar planning ko kuma haka kawai? Muna da ingantaccen maganin rashin haihuwa ga mace da namiji, wanda za ki bada sadakar 2k ga matsalar ko wane ɓangare. In sha Allah za ki dawo da godiyarki bayan amfani da maganinmu. Sanyi (infection) ne yayi miki yawa yake saka ki ciwon mara, zubar farin ruwa, ƙaiƙayi, ƙuraje, ɗauke ni'ima, har ma ya saka mijinki ya dinga miki gani-gani saboda bakya gamsar da shi? Da naira 3k zamu haɗa miki magungunan da za kisha ke da Oga in dai kika yi amfani da su ku da sanyi har abada in Allah ya yarda. Muna sayar da ingantaccen haɗin sabaya, wanda zai sa nonuwanki su cicciko, hatta fatar jikinki sai ta murje sanadiyyar shan kunun sabayarmu. 2500 bokiti 1litter. Muna da maganin wankin nono ga mai ciki da mai shayarwa, wanda indai kikai amfani da shi yaronki zaiyi tubarakallah, ba ruwanki da laulayi. Muna da ingantaccen maganin Daji (Cancer), typhoid, maleria, yaron da yayi nauyin ƙafa, da sauran cututtukan da ban ambata ba. Muna aika maganinmu ko ina tsakanin Nijar da Nigeria, ga masu buƙatar magani da gaske su tuntuɓeni akan lambar wayata 07039080978, ko 09077591726 Noted: *MAI SON MAGANINMU IDAN BA A KADUNA YAKE BA, SHI ZAI YI KUDIN MOTARSA HAR ZUWA INDA YAKE, BABU INDA BAMA TURAWA IN SHA ALLAH.....SAI KUN ZO* 💔💔💔💔❤‍🩹❤‍🩹💔💔💔💔 *DA CIWO A ZUCIYATA* 💔💔💔💔❤‍🩹❤‍🩹💔💔💔💔 _MALLAKIN_ *SAJIDA NIJAR* *FREE BOOK NE* 1️⃣5️⃣ LITATAFAN MARUBUCIYAR Duk karyar kada Yar mahaukaciya Neman na kaina Bani da zabi Bak'a ce Kutkale Makauniya ce Mage Duk nisan jifa Idan ka raina inda kake Dutse Alkalamin kadarata Bani da zabi Dakika Biyar Now *Da CIWO A ZUCIYATA* *Tallah, tallah, tallah* *SECRET DE LA FEMME DU MANGA* _Gidan Kamshi, Sirrin Manyan Mata, nesa tazo kusa,Amarya ,Uwar gida,Ango da mai gida Har ma da yan mata da samari shin kuna sane da cewa HAJIYA FUSAM ta shirya tsaf domin gwangwaje ku da turarakunta masu dankaran kamshi? Tare Kayan gyaram jiki na musamman ,wanda daga nesa kamshin ki kadai ya wadatar ya isar da sakon zuwanki waje,gidan ki kuwa sai ya zam abun kwatance wajen kamshi, kar na cika ku da surutu bara in fara zayyano su_ Farar Humura Bakar Humura Humura special, humura de bain Humura epicé Lait de nuit Parfums désodorisant Parfums rideau et dras Lait de nuit Alkam Kulakcam *Waɗannan kadan ne daga bangaren turaran ruwa* Gagab, sandal flex, Durot, durus, sandal fleur, tafarce, farce, sandal bangui, sandal, hypotonic sandal, al'ut, coktail creation VIP, Gajiji, Mankaji, turaran wutar labule da cafet, Aba malan, boulettes *Munada bangaren gyaran jiki kamar haka:* mai mai saka santsin jiki, mai mai kanshi, Kayan gyaran jiki mai saka fata ta yi santsi da laushi, kayan gyaran jiki mai saka fata ta yi fari, Sabulu mai saka fata ta yi haske, sabulu mai saka fata ta yi santsi, sabulu mai goge yanayin fata, mai wanda baya saka fari mai gyara fata Sayen na gari mai da kudi gida,sai an gwada akan san na kwarai💃💃 Hajiya Fusam na zaune a kasar Niger domin yin magana da ita kai tsaye tuntuɓi wannan number 97 82 44 94 *SECRET DE LA FEMME DU MANGA* Gidan Kamshi, Sirrin Manyan Mata💃💃💃💃💃 Kanta ta dauke a hankali daga dubansa ta kama marfin motar itama ta fice du jikinta wani sakaka ta nufi soron gidansu kunnayenta basu jiyo mata tashin motarsa ba har ta shige cikin gidan A hankali ya dan dafe gabn goshinsa cike da tunanin abubuwa da yawa da suka shafi rayuwarsa a yau din nan Ajiyar zuciya sanyayiya ya sauke sannan ya tayar da motarsa ya nufi gidansu, zuciyarsa cike da tunanin wanka ne ya dace da shi da kuma nutsatsen hutu, ama wani abu a cen kasan zuciyarsa na fada masa cewa eh lalle wanka da hutu mai sunnan hutu ne suka dace da shi, a yau shima Taufeek bayan dogon jira da dogon daukan rayuwa irin ta gwauraye ya zama ango, ya zama magidanci...........tabas wannan rana ya dace ya yi hakuri da duk wani abin da zai iya taba masa zuciya ya fuskanci sabuwar rayuwar dake gabansa Bai samu isa gidansu da wuri ba, sai da ya yi yan biye biyensa ya samo guzuri irin na cikaken ango sannan ya karasa A cikin motar ya bar komai ya fice ya nufi bangaren mahaifiyarsa dake cikin zuciyarsa Mutanen dake falo baba basu fi a irga ba, dan kowa gajiya ta kai shi ya nemi waje ya tsugunar da hakarkarinsa dan samun hutu Sama ya haura ya karasa kofar dakin mahaifiyarsa A nutse ya bubuga sannan ya yi salama ya kuma saurara Jin muryarta tan amsa salamar ya saka shi bude kofar ya shiga yana sake dan dubawa har ya dawo da dubansa kanta yana dubanta Murmushin ya saki shima, kamar yadda fuskar mahaifiyarsa ta fitar da sansanyan murmushi mai tafe da sakwani kala daban daban A hankali ya karasa ya zauna daf da ita ya harde kafafuwansa ya ce" Barka da warhaka Umana" Murmushin ta yi itama tana sake dubansa ta ce" Daga ina kake haka? Ko guduwa ka yi irin na Fulani?" Yar dariya ya yi yana girgiza kai ya ce" Su Khausar na mayar gida ai" Itama ta yi dariyar , sannan ta sauke ajiyar zuciya a sanyaye ta zubawa fuskarsa ido Bata da bakin magana a yau face ta godewa Allahu sarkin samai da kasai, wanda ya halici bawa ya kuma saka masa jarabawa kala daban daban a tsanin rayuwarsa Ita dai jarabawarta abokanan zamanta ne a kan d'anta, a da zamansu sunna yi ne komai shawara guda, ita bata bin malaman tsubu ko bokaye bale ace a cen ta jiyo abinda ya tsotatata da su, yau da gobe ne d babu abinda ta bari ya saka ta wayi gari ta ringa tsintar abubuwan da suke yi a bayan fage wa'inda suka girgiza tunaninta suka tsotatata har suka saka ta dauki wannan dabi'a ta kadaice kanta ya zamto idan ka ji muryarta a falo mijinsu ya bukaci haka ko d'anta ya bukaci haka, sai ko idan baki ta yi , yawancin lokuta ta fi tarewa bangaren Hajia dan ta fi sakewa , ita din mutun ce mai gudun munafurci, idan ta zauna da kai da zuciya daya ka ringa munafuntarta lokaci daya zaka nemi wace ka sani ka rasa, sam zaka kasa gane kanta, tana iya shafeka a babin bil'adaman da idannuwanta suke da hurumin gani a gabanta, dalilin da yasa tsakaninta da matan baban Taufeek mutunci gaisawa bayan wannan kowa ya rike abinda yake hurumi a gareshi A sanyaye ainun ta ce" *MAGIDANCI* " Idannuwansa ya dago daga kunce agogon hannunsa ya dan zunawa fuskarta ido jin ta ambaci sunnan da hajia ke kiransa da shi A hankali ta ci gaba da fadin " Yanzu na raka Hajia, a yau lakabin da take maka cewa MAGIDANCI ya cika Autana" Dan tsai ya yi dan alamu da yake gani na tana son yin kuka Kansa ya cire kasa kasa sosai ya ce" Bafa gidan miji za'a kaini ba fa ake son rikitani ina zaman zamana, Matar babana kuka za'a yi?" Daria ta saki ta miko hannunta tana dungure kansa ta ce" kai ba zaka barni irin dan kukanma na taba ba?, Haba Baban yara" Shima yana dariar ya rike hannayenta duka biyu yana dubanta ya ce" Da izinin Allah, in ina raye, kuma ina kusa, kuka sai dai idan ya shamaceni ya samu fuskar mahaifiyata" "Allah ya yi maka albarka, tabas na yarda cewa daya tak gari ne, kuma mai albarka ake nema ba wai tarawar ba a tara mararsa albarka, Taufeek ina matukar alfahari da kai, ina kuma gannin kokarinka, kaine ASIBITIN KA, kaine KASUWAR MAHAIFINKA, kaine hidima wa al'umarka, ina matukar alfahari da kai, ina fatan Allah ya dafa maka duniya da kiyama........, Ka ga yau burina ya cika, a da idan na dan dubeka sai na ga shekaru fa ja suke, shekarunka tafiya suke yi, ama maganar aure shiru kake ji , ashe kamar yadda Hajia ta fada ne lokaci ne mu naka dama gashi yau Allah ya yi, Allah ya sa iyalinka ta zamto cikon farin cikinka duniya da kiyama" Maman Taufeek ta fada a sanyaye ainun tana mai dan jimke haannunsa dake karra tabatar masa maganar daga zuciyarta take fitowa A hankali ya sada dubansa, sannan a hankali ya amsa da amen ya Allah, sai kuma ya sake dagowa yana dubanta a lokacin da ta ci gaba da fadin" Taufeek du shekarunka, da iliminka, wajibunmu ne idan muna raye mu ringa tunatar da kai da kuma yi maka nuni a kan abinda ya dace da rayuwarka dan samun rabauta a wajen ubangijinka, ka ga aure baa abin wasa bane, a yanzu wani nauyi mai girman gaske ya rataya a wuyanka, wanda ba wai iya ka ciyar kaa shayar ka tufatar bane kawai, harta maganar baki idan har domin Allah zaka zauna da iyalinka ya dace ka ringa tauna harshe kafin furucinka a gareta, kuma ka kiyayi shiga hakinta ko wani iri, ka yi kokari kaa koyar da ita yadda kake so ta kasance cikin salama ba da wulakanci cin zarafi ba, domin ka ga mace , makarantar da ka sakata a zamanta da kai karatun zatai maka bita har ku koma ga ubangijinku, ina nufin idan ka gyara kanka ka gyarawa, idan kuwa ka bata kanka ka batawa ka ji Taufeek?" Kai ya gyada, a hankali yana sauke ajiyar zuciya, sosai yake daukan karatun mahaifiyarsa a ko yaushe, ya kasance mai matukar ba hudubarta mahimmanci, bata taba budar bakinta idan sun yi zama irin wannan ta koyar da shi mugun abu ba, shi yasa yake girmama dukkan furuci nata koda kuwa cikin wasa da dariya zata yi masa "Shin yaushe ne aikin nan da kake yi zai kare?, Shekara nawa kennan bana?" Ta fada a nutse tana dubansa da kula Yar ajiyar zuciya ya sauke a hankali ya ce" In sha Allah inaga dole sai na karra wasu yan watani a makarantar , domin an samu wasu ba'a samu wasu ba, " Mahaifiyarsa ta ce" Ama yaya zaka yi da sanninka da aka yi da sunnanka da kuma yannayinka?, Taufeek aikin nan wani lokacin ni tsoronsa ke kamani kar aje a bincikeka a san wanene kai, yanzu haka ina gannin mamakin manyan makarantar ace basu ganeka ba?" Da kula sosai ya ce" Mama, ai basu san da zamana a makarantar ba, abindama ya sa na zabi hakan kennan, dan yawancin lokuta mutun kan hangi matsalarsa a nesa ne bayan tana daf da hancinsa, ba zasu taba sakawa ransu cewa ni zan iya shigarsu a haka, sai dai ya zame min wajibi na yi domin nima sheda ne an kawo min daidaikun daliban da suka ringa rikita min patin wa'inda makarantar ta yaye, abinda ya fi dan sakani dakatawa a tafiyar nan shine rikita rikitar da nake ciki na amsoshina barkatai, shin laifin na wanene a ciki? Daliban ne, ko malaman, ko kuwa masu rike da makarantar? Idan aka yi duba da wasu daliban cikin makarantar nan za'a sha mamakin tarin baiwar da Allah ya masu, kin ga ai Khausar na daya daga ciki, na san wacece ita a fannin karatunta, a yanzu haka na tsame takardarta zan turata ne hospital baba ta je ta idasa gogewa a aikinta, hakn na nunin idanma akoy maganar malaman kansu akoy masu wasa to fa akoy jajirtatu dan dalibi ba zai koyar da kansa abinda yake bako da girma irin na asibiti kai tsaye ba, ina dai cikinsu yanzun matsayin malami ne zan dauka dan har an gama gyara komai" Cike da kula itama Maman ta ce" Allah ya tsare, Allah ya sa a samu abinda ake nema, kuma Allah ya bada ladan taimako" A saman lebensa yake amsawa da amen, ya dan karra jimawa a wajen Maman sannan ya mike ya tafi, Mama kuwa ta bishi da addu'a a zuciyarta tana ji inama ace ya ajiye aikin nan? Sai dai ta san abu ne da ba zai yiwu ba dan ta san yaronta da tsayuwa kan abinda ya saka a gaba, bale wannan din aiki ne na samun lada dan kuwa idan har ba'a gano ina matsalar take ba tsaf za'a yi ta kashe al'uma dan son zuciya da dan kudin da bai taka karra ya karya ba, ta san bama zai yarda a masa maganar bari ba, ai yama jima a ciki kai tsaye ba zai janye kansa ba, abinda ka ga mai Kwanoni ya hakura ya bar Taufeek a ciki ka san mai mahimmanci ne Gidan ya sake daukan tsitttt, ba motsin kowa ba na komai Wayarsa ke kange a kunnensa yana amsa kiran mahaifinsa sunna dan zantawa, duba da yannayin daren da ya tsala ga kuma yau din ba mahaifiyarsa ce da aiki ba ya sa ya yi kiran mahaifin nasa wanda shima ya takaita firar tasu yana mai sanar masa zasu hadu da safe idan Allah ya nufa Da wannan ya karasa kofar nasa bangaren Bangaren da aka saka iyalinsa, bangaren da aka yiwa gyara na musaman, waje mai nisa da wajen iyayensa sai dai duka a cikin gida guda ne A sanyaye ta yi salama bayan ta daga kiransa Dan lumshe idannuwansa ya yi a hankali ya ce" Shin amaryana ta yi barci ne?" Yumnah dake zaune da kawayenta biyu, sai wasu daga cikin familly dinsu da suke tare da ita zasu yi mata kwanakin da ake yiwa amarya a al'adance ta dan shagwabe fuska tana sake kallon agogo har karfe daya ta gota fa, tun kwaliyarta na walwali har ta disashe bai karaso ba, bayan ance idan aka kawo amarya wani angon a dakin yake salatar isha tare da amaryar dan zumudi da farin cikin kasantuwarta a tare da shi a darensu na farko a tarihi ta ce" Aa bamu yi barci ba" Dan tsai ya yi jin basu yi ba, maimakun bata yi ba, ya zata zuwa yanzu yan rakiyar nata sun yi barci shi yasa yake son lekawa ya ga lafiyarta da yar tsarabar da ya riko mata, ama kuma tunda ya riga ya zo ai ba zancen juyawa "Ina kofar falo" ya fada a nutse sannan ya kama kofar ya murda da sallama a bakinsa kasa kasa sosai kamar yadda ya saba Du juyowa suka yi sunna amsa salamarsa Da sauri cousint sister dinta ta rufa mata mayafinta a kanta tana fadin" Ke yaya zaki bude bayan zaman jiran ya sayi baki muke? Oyoyo angonmu ama gaskiya ka san dole ka sayi bakin nan da tsada dan ka jima a waje" Da dan mamaki ta dago tana kallon Basira, ya salam, tana cewa basu jima da ta gama kwatanta masu kar su masa irin wasan nan ba, in kudin ne su bari zata amsa masu? Ama basira har wani zakalkalewa take yi jiki na rawa tana ta zuba? Mamaki bai gama kasheta ba sai da ta ga Basirar ta amso abubuwan hannunsa, a nan ta so budar baki dan yin magana , harufan bakinsa cikin kamala da kula da tsare hakoki irin na adininsa suka dakatar da ita a lokacin da ya yi maganar cikin dan murmushi sannan ya shige ciki bayan ya nemi afuwa da fadin lalle ba maganar neman ragi ko nawa yar uwarsu ta yanka ya siya in di baki ne Yana shigewa ta juyo a dan hasale tana duban su Basira su dukansu, domin ido suka ringa zarowa kowace na tofa albarkacin bakinta a kan Taufeek din, maganganunsu irin lalle ta dauko zazafa, ashe a kusa da kusa da shi ya fi cika ido, ga halin girma dan kyauta na sakawa a ga tsayin Wada, a cikinsu kawarta daya ce tak bata ce komai ba, ita kuwa kamar barci ne ke kwasarta ko me? Takaicin hakan ya sakata girgiza kai ta nufi cikin a ranta tana ayana da ace dare bai yi ba tsaf zata nemi hanyar rabuwa da su, itafa bata haka a kan Taufeek, Ledojin da ta shigo da su ya dan bi da kallo a lokacin da ta shigo dakin ta so nufar wajen table dan ta ajiye *ALLAH BAI SAUKAR DA CIWO BA SAI DA YA SAUKAR DA MAGANINSA* Ni ce dai Fareeda Abdallah, na sake dawo muku da tallen magungunanmu da zuwa yanzu bazan iya ƙayyade yawan waɗanda suka dace da biyan buƙata sanadiyyar amfani da maganinmu ba. Alhamdulillah! Ƴar'uwa ki gwada, wataƙila warakarki na tattare da maganinmu. Haihuwa ce baki taɓa yi ba ko kuwa jinkiri kike samu sanadiyyar planning ko kuma haka kawai? Muna da ingantaccen maganin rashin haihuwa ga mace da namiji, wanda za ki bada sadakar 2k ga matsalar ko wane ɓangare. In sha Allah za ki dawo da godiyarki bayan amfani da maganinmu. Sanyi (infection) ne yayi miki yawa yake saka ki ciwon mara, zubar farin ruwa, ƙaiƙayi, ƙuraje, ɗauke ni'ima, har ma ya saka mijinki ya dinga miki gani-gani saboda bakya gamsar da shi? Da naira 3k zamu haɗa miki magungunan da za kisha ke da Oga in dai kika yi amfani da su ku da sanyi har abada in Allah ya yarda. Muna sayar da ingantaccen haɗin sabaya, wanda zai sa nonuwanki su cicciko, hatta fatar jikinki sai ta murje sanadiyyar shan kunun sabayarmu. 2500 bokiti 1litter. Muna da maganin wankin nono ga mai ciki da mai shayarwa, wanda indai kikai amfani da shi yaronki zaiyi tubarakallah, ba ruwanki da laulayi. Muna da ingantaccen maganin Daji (Cancer), typhoid, maleria, yaron da yayi nauyin ƙafa, da sauran cututtukan da ban ambata ba. Muna aika maganinmu ko ina tsakanin Nijar da Nigeria, ga masu buƙatar magani da gaske su tuntuɓeni akan lambar wayata 07039080978, ko 09077591726 Noted: *MAI SON MAGANINMU IDAN BA A KADUNA YAKE BA, SHI ZAI YI KUDIN MOTARSA HAR ZUWA INDA YAKE, BABU INDA BAMA TURAWA IN SHA ALLAH.....SAI KUN ZO* 💔💔💔💔❤‍🩹❤‍🩹💔💔💔💔 *DA CIWO A ZUCIYATA* 💔💔💔💔❤‍🩹❤‍🩹💔💔💔💔 _MALLAKIN_ *SAJIDA NIJAR* *FREE BOOK NE* 1️⃣6️⃣ LITATAFAN MARUBUCIYAR Duk karyar kada Yar mahaukaciya Neman na kaina Bani da zabi Bak'a ce Kutkale Makauniya ce Mage Duk nisan jifa Idan ka raina inda kake Dutse Alkalamin kadarata Bani da zabi Dakika Biyar Now *Da CIWO A ZUCIYATA* *Tallah, tallah, tallah* *SECRET DE LA FEMME DU MANGA* _Gidan Kamshi, Sirrin Manyan Mata, nesa tazo kusa,Amarya ,Uwar gida,Ango da mai gida Har ma da yan mata da samari shin kuna sane da cewa HAJIYA FUSAM ta shirya tsaf domin gwangwaje ku da turarakunta masu dankaran kamshi? Tare Kayan gyaram jiki na musamman ,wanda daga nesa kamshin ki kadai ya wadatar ya isar da sakon zuwanki waje,gidan ki kuwa sai ya zam abun kwatance wajen kamshi, kar na cika ku da surutu bara in fara zayyano su_ Farar Humura Bakar Humura Humura special, humura de bain Humura epicé Lait de nuit Parfums désodorisant Parfums rideau et dras Lait de nuit Alkam Kulakcam *Waɗannan kadan ne daga bangaren turaran ruwa* Gagab, sandal flex, Durot, durus, sandal fleur, tafarce, farce, sandal bangui, sandal, hypotonic sandal, al'ut, coktail creation VIP, Gajiji, Mankaji, turaran wutar labule da cafet, Aba malan, boulettes *Munada bangaren gyaran jiki kamar haka:* mai mai saka santsin jiki, mai mai kanshi, Kayan gyaran jiki mai saka fata ta yi santsi da laushi, kayan gyaran jiki mai saka fata ta yi fari, Sabulu mai saka fata ta yi haske, sabulu mai saka fata ta yi santsi, sabulu mai goge yanayin fata, mai wanda baya saka fari mai gyara fata Sayen na gari mai da kudi gida,sai an gwada akan san na kwarai💃💃 Hajiya Fusam na zaune a kasar Niger domin yin magana da ita kai tsaye tuntuɓi wannan number 97 82 44 94 *SECRET DE LA FEMME DU MANGA* Gidan Kamshi, Sirrin Manyan Mata💃💃💃💃💃 Ajiyewar ta yi sannan ta juyo saman kujerar da yake zaune ta zuba masa ido Murmushi ta saki a bayane ta rufe fuskarta da hannayenta biyu, domin idon da ya zuba mata sai da ta ji har kasan zuciyarta wani irin zirrrr mai kama da tashin tsigar jiki da kuma wani irin nauyin idannuwansa a fuskarta Murmushi ya yi a hankali ya dan miko hannunsa kasa kasa ya ce" Zo " Kamar jira take yi ta daga kafarta da sauri ta karasa ta fada jikinsa tana sake rufe fuskarta a kirjinsa ta saki ajiyar zuciya bayananiya A hankali ya mayar da dayan hannunsa ya rungumeta a jikinsa shima nasa idannuwan a lumshe Kasa kasa sosai ya ce" Na fa yi dati zaki gogi dati a kwaliyarki mai kyau" Idannuwanta ta sake lumshewa a hankali ta ja numfashi kadan tana jin kanshin turaran jikinsa mai sanyin kanshi na shiga hancinta kasa kasa ta ce" Bana jin wani dati, Ya Taufeek i'm so happy today " Hannunsa ya saka ya dago fuskarta ya zuba mata ido Ya yi murmushi a hankali ya kai lalausan lebensa saman goshinta ya mana mata kisss din da ya sakata sake lumshe ido Kasa kasa ya ce" Ina maki barka da shigowa rayuwana Yumnah, Allah ya bamu zaman lafiya" "Amen ya rab" ta amsa ita dinma, sannan ta sake zubawa sajensa ido kamar ta sake rukunkume shi haka take ji A nutse ya ce" Bara na koma" Ido ta bude da sauri tarr ta dora saman fuskarsa Ya koma? Ina? Kasa hakuri ta yi gannin da gaske yake ta ce" Ama ina zaka je ne da daren nan Yah Taufeek?" Da kula sosai ya ce" Ba zan kwana a nan ba sai an gama bukukuwa irin na al'adun nan, you see da kunya na ringa tsalake mutane ina shigowa kuma ina fita" Wani irin makoko da dana sannin barin wadincen rubda rubdan rubabun banzan kwanar mata a yau ya sake shake mata wuya, innalilahi tafia zai yi ? Du irin wankin kwakwaluwar da ta sha na irin kulawar da zata bashi daga yau har karshen rayuwarta dan kar ya dubi kowace irin mace haka zasu wani wargaza mata niya? Wace ta yi mata gyara ta yi mata wankin ido mai matukar girma domin mahaifiyarta ta nemi hakan, an sakarwa matar kudi na mamaki da ya saka ta zage dantse ta yi mata dala dala cewar sai ta ki jikinra ta sakar masa jiki ta yadda babu wata banza da zata shiga zuciyarsa sama da ita, har fada mata ta yi kar ta saki dan tana budurwa tace zata masa raki, komai wahalar da zata sha ta jure ta mike kamar ba ita ba, kuma ta yiwa kanta alkawarin jurewar sai kawai yace zai kwana ba a nan ba? Tana ji tana gani, mijinta ya yi mata salama bayan ya dauko ledojin da ta ajiye ya damka mata cewar na baki ne sannan ya fice ya nufi bangarensa cikin nutsuwa Nan ta zubar da ledojin ta karasa saman shinfidarta da aka yane da farin abin shinfida mai tsada aka baza turaran girma da kannanun flowers masu kanshi sai daukan ido suke ta hau ta kwonta tana rintse idannuwanta hawaye suka shiga bin gefen kuncinta cike da bacin rai ta kasa koda komawa inda suke bale har ta wani kai masu abin ledar cen, hasalima itama yinwar take ji, ama wannan abu da ta shaka ya sa ta ji ta hakura da jin yinwar, ama da bakin naci sai da Basira ta tardota har nan tana faman tsokanarta cewa angon ya fice ya masu sai da safe ita kuma ta makale ko zumar soyaya aka lasa mata? Ta fito mana, Cike da rashin walwala ta nuna mata cewar ta gaji ne barci take son tabawa ga sakon nan ta je masu da shi inji shi, ita ta kwonta sai da safe Da wannan ta yi kwonciyarta ta barsu da surutu tsakaninsu da baje bajajar suka auna a tumbinsu sannan suka kama wajen kwonciya dan hutawa A nutse ya karasa bangarensa Kamar yadda yake jin har wani mintsininsa datin jikinsa ke yi direct bayi ua wuce da babaan tawul dinsa a kafadarsa bayan ya cire rigar jikinsa Ya dauki lokaci a ciki sosai kafin ya fito a nutse ya karasa wajen wrdrn dinsa ya ciro jalabiya ya saka sannan ya saka gajeran wando ya karasa wajen salaya dan gabatar da shaf'i da wuturi Yana gamawa falo ya koma da laptop dinsa, da kuma wayarsa baba sai dan abin rufa da ya janyo domin niyarsa a cen zai yi barcinsa, dan dole sai ya duba laptop din ya yi yan aiyuka masu mahimmanci sannan ya kwonta A lokacin da ya zo dan cin abinci kamar wayarsa ta fado cikin ransa Tsam ya yi yana tunanin inda ya sakata, domin gaba daya ya manta da ita a cikin kwakwaluwarsa Rigarsa da ya cire har ya ajiye saman mashine din wanki ya koma ya lalube, sai dai babu A hankali hoton wayar a hannun KHausar ya shiga dawo masa idannuwansa Idannuwansa ya lumshe ya koma falon sannan ya dauki wayarsa baba ya saka numbar sekatarinsa ya yi kiransa A nutse ya sanar masa cewa kar a tura sakon komai a karamar wayarsa ta fice a hannunsa Sakatarin ya sanar masa cewa ba'a rigai aka tura wani baban sako ba, wanda aka tura na marar lafiyar nan da aka dauko daga kauye ne kawai, ana iya nunin an bacewa lamba idan yana so? Dan shiru ya yi, kafin ua girgiza kai yana fadin kar a ce komai, sannan ya kashe wayar ya karasa wajen cin abincinsa ua zauna dan cika kulunsa ______________________________________ Washe gari da wuri wuri Khausar ta shirya ta fice a gidansu bayan babanta ya bata dari biyuntata nufi cen wajen da ake kafa sunnayen wa'inda zasu iya zuwa su amshi takardunsu da wajen da zasu amsar Sai dai tunda ta je din hankalinta ya nemi rikicewa sakamakon rashin gannin sunnan TAUFEEK a layin wa'inda aka tabatar cewa sun samu din bayan ga sunnan du wani wanda ta ji ance ya samu ciki harfa ita Takardar nan ta mata karantawa ta fi a irga har sai da ta fara shanye sunnayen dake laye ta hakura ta juyo gida ido sai zubar da ruwa yake tana tafe tamkar zata tashi sama, uwa uba yau din hijab din Mama nema ta saka du irin kwaliyar da aka sha jiya kamar ba a fuskarta ba fuska tana neman sinkime mata dan shiga rudani da tunanin me kennan? Tana shigowa a lokacin har karfe goma na safe ta gota ta nemi waje ta shiga rusawa Mama kuka kan ai Besty fa da alama bai samu ba, dan bata ga sunnansa ba Itama Maman hankalinta ya tashi gaskiya, dan harma ta rasa to me kennan? Aisha ce ta ringa kwatanta masu to ko dai an mance ne, ana samun irin haka fa kar su yi hahawar rikicewa, ama ina Khausar kaffafuwa baje a tsakar gida kukanta take kashirban da kyarma ta iya cin maka yar murden da Aisha ta silala tana faman bin Aishar kan ta zo ga dari biyunta nan ta siyo kati a kireshi Mama ne ta hanna hakan, cewarta jiya fa yake ango, kar su kireshi bata so A dole Khausar ta hakura da maganar kiran, sai dai nata sunna da ta gani gaba daya zumudinta da farin cikinta suke neman bacewa bat, abinda ya fi damunta in har bai samu ba fa yaya zai ji? Yaya zasu yi? Sam ta manta fushin da take yi da shi, burinta ta ganshi su je su sake dubawa su ga ta inda zasu bilowa al'amarin Kusan karfe biyar na yama sunna zaune su uki a tsakar gidan ya shigo bakinsa dauke da salama Mama ce ta fara amsawa fiskarta wadace da fara'a tana sake rufe jikinta da hijab dinta sosai tana masa maraba da zuwa Dukawa yayi kamar yadda ya saba ya gaishe da Mama sannan ya yi zamansa saman tabarmar da Aisha ta sake kabewa ba wani kyankyami ko wani dari dari yana duban kwanon dake gaban Kausar tana dibar awara ta kudinta na safe ya mika hannu ya ja gabansa shima ya shiga ci hankali kwonce a lokacin da Mama kuwa ta mike ta yi ciki dan bata cika zama idan sunna nan ba, ba dan komai ba sai dan akoy yan matan, a tare da su baki daya Khausar ta nemi sake dauko rikicewar fuskarta tana kallonsa ta ce" Wai freind daga ina kake? Ka kuwa san tunda safe nake nan ina sheka kuka ina nemanka?" Kumatunta da suka dauki abin man awara ya bi da kallo, sai kuma ya tabe baki kasa kasa ya ce" Haka fa, gashi kina dirkar awarama " Awarar ta kalla, ta kalli hannunta, sai kuma ta kalli Aisha ta ce" Aisha, dan Allah ban yi kuka ba?, Awarar nanma da ka gani ji na yi juwa zata makani da kas ne na yi hakuri nake ci, ama ni dake cikin tashin hankali, zuwa fa na yi ban ga sunnanka ba , ka san me hakan ke nufi ai ko?" Cikin halin ko in kula ya ce" Eh" Hakan ya sa ta zuba masa ido, wani abu na dan mintsininta a zuciya, EH? EH fa yace ko? A dan yannayin fusata ta ce" Eh?, Wani irin eh? Hakan fa na nufin baka samu ba ko kuwa an cinye maka ne, dan ai da aka fada an fada ka samu ko?" Banza ya mata, maimakunma ya bata amsa sai ky din mota da ya mikawa aisha ya umarceta kan ta dauko ambulop a motar Jim kadan ta dawo Lhausar ta cika yadda ka san an saka mata balan balan a kumatun an hura sai hararensa take yi, shi kuwa har awarar tata ya kama sai cinyewa yake yi ko damuwar abinda ta fada bai nuna ba Ambulop din ya yiwa Aisha nuni da ta bata Tana budewa ta ga takardarta, watau diplomanta ta kwalin bama ta takardar ba, wace in kana son amsarta bayan ka yi takarda ka ajiye sai ka yi jira har Allah ya fitar maka da ita, dan kuwa kai tsaye ba zaka je ka amsa ba, Bama wannan na, a yau aka kafa masu cewar suna iya amsa, hakan na nufin daga gobe masu hanya zasu iya zuwa su samu ta takardar, ya su ya su kuwa sai sun bi layi har layinsu ya iso, sai takardar dake nunin an nata damar zuwa koyon aiki a babar hospitall din garin har na tsayin wata uku da albashi du karshen wata na kudin abin hawa da abinci Galala take rike da takardar baki da hanci da ido a bude a lokacin da Aisha le zuba masa ruwa yana wanke hannunsa sannan ya dauki piyawatan dake gefenta ya huda ya shiga sha hankali kwonce A dan tsorace da shi ta ce" TAUFEEK? Me nake gani haka ne?" Hannunsa ya dan daga mata har sai da ya kare ya wani lumshe ido kamar ya sadu da kaza lafiyayiya yankan hausa silalar murhu sannam ya dubeta a nutse ya ce" Ina cin abincin kike so na maki magana ko me?" Khausar ta sake dubansa, sannan ta miko masa takardar kamar ba san meye ba tan kallonsa ta ce" Kalli fa, takardana ne, a in ka samo? Kalli Wannan fa, hospitall fa?" Takardar ya amsa shima ya duba kamar bai san me aka rubuta ba, sannan ya kade tunanin ta hanyar dubanta ido cikin ido ya ce" Eh , Aba ne ya bani dazu, Khausar nima Allah ya nunan an amso min tawa haka, jibi rubutun yassss yasss masha ALLAH " Dubansa take yi kamar bakon halita a gabanta, maganarsa da Hausa yake yi sai dai sam tana neman shige mata, ABA? eh lalle ta san mahaifinsa baban mutun ne mai dama sosai a duniya, sai dai haka kawai take ta tunanin ta yaya? Aban nan fa jiya ya yi taro na mamaki a gidansa, yau sai kawai ace ya amso mata takarda? Bayan wannanma to Aban ko dai yanada wani mukami a fannin asibiti ne? Ko tace siyasa ne? Dan abin ai kamar ya shafi baban wajen ilimin asibitin ne kai tsaye ba wai kasa kasa ba "Rashin gannin sunnana ne ya saka shi dan bincikawa har cen, daga nan ne na fada masa a biyo da naki takardun" ya fada yana dauke dubansa a yannayinta, a zuciyarsa kuwa yana tunanin me kennan yake fada? Ya zauna yana fadin magangannun da gasunnan dai? Koda yake yana da hujarsa Farin ciki ne ya mamaye gurbin wasi wasin da ta nemi shiga, harma ta dafa ta mike da dan gudu ta nufi dakin Mama tana fada mata abinda yake faruwa Murmushi ya yi kasa kasa ya dauke dubansa a kanta ya maida kan wayarsa har Maman ta fito sai godiya take masa shi kuwa ya nuna a daina godiyar haka Karshe dai kamar yadda ya saba share kafa haka ya yi zamansa , har sai da ya fito daga sallar magariba sannan ya shige mota da niyar tafiya A lokacin ne da kula ya ce" Besty, ni jiya baki ga wayata karama ba?" Khausar ta dan zarro ido, sai kuma ta ce" Lah, tana dakin Aba, bara na dauko maka, nama manta da muna fada da kai, yanzu tsakani da Allah Taufeek fada ne ka yi a titi da mutumen da kana ganninsa ba a cikin hayacinsa yake ba? Haba dan Allah wannan sam ai ba wani anfani, bai dace ba, gaskiya kar na kuma jin haka gaskiya" Wasu hannayenta mundil mundil da take juyawa tana masa kashedi yake kallo, kafin ya tabe baki a ransa ya ayana' To Mama, ke da hajia ban san waye ya fi wani neman kaini bango ba' A bayane kuwa sai ya yi murmushi yana kallonta har ta shige ciki A lokacin da ta dauko wayar haka kawai ta samu kanta da dannanwa, daidai tana fitowa take karanta sakon dake saman wayar, sako ne kamar haka *ASALAMU ALAIKUM INSPECTOR, MUN DAUKO MATAR DA KA BADA DAMAR A KAWO ZAKAI MATA TIYATA WACE HAJIA KHADIJA TA KAWO MAGANAR TANA SON TALAFIN NAN TA KUNGIYAR TAIMAKO, MUN MATA GWAJE GWAJEN DA ZAKA TAMBAYA, MUNA JIRAN JIN RANAR DA ZAKA SAKA DA KUMA TREATEMENT DA ZAMU YI MATA KAFIN KA SHIGAR DA ITA DAKIN TIYATAR* Message din take kallo kamar tana son sake aro yaren ABCD dan ta fara fahimtarsu kafin ta durmiya a duniyar yaren turanci uwa uba ta kai yaren dake saman wayar A hankali ta dago daga dokin kofar gidan da take tsaye ta zuba idannuwanta a saman fuskarsa, a lokacin shi kuwa jikinsa ya bashi abinda ta gani, sai ya dauke dubansa ya yi alamun ita yake jiran nan Dan juyowa ya yi da alamun a dan kagauce yake ya ce" *ALLAH BAI SAUKAR DA CIWO BA SAI DA YA SAUKAR DA MAGANINSA* Ni ce dai Fareeda Abdallah, na sake dawo muku da tallen magungunanmu da zuwa yanzu bazan iya ƙayyade yawan waɗanda suka dace da biyan buƙata sanadiyyar amfani da maganinmu ba. Alhamdulillah! Ƴar'uwa ki gwada, wataƙila warakarki na tattare da maganinmu. Haihuwa ce baki taɓa yi ba ko kuwa jinkiri kike samu sanadiyyar planning ko kuma haka kawai? Muna da ingantaccen maganin rashin haihuwa ga mace da namiji, wanda za ki bada sadakar 2k ga matsalar ko wane ɓangare. In sha Allah za ki dawo da godiyarki bayan amfani da maganinmu. Sanyi (infection) ne yayi miki yawa yake saka ki ciwon mara, zubar farin ruwa, ƙaiƙayi, ƙuraje, ɗauke ni'ima, har ma ya saka mijinki ya dinga miki gani-gani saboda bakya gamsar da shi? Da naira 3k zamu haɗa miki magungunan da za kisha ke da Oga in dai kika yi amfani da su ku da sanyi har abada in Allah ya yarda. Muna sayar da ingantaccen haɗin sabaya, wanda zai sa nonuwanki su cicciko, hatta fatar jikinki sai ta murje sanadiyyar shan kunun sabayarmu. 2500 bokiti 1litter. Muna da maganin wankin nono ga mai ciki da mai shayarwa, wanda indai kikai amfani da shi yaronki zaiyi tubarakallah, ba ruwanki da laulayi. Muna da ingantaccen maganin Daji (Cancer), typhoid, maleria, yaron da yayi nauyin ƙafa, da sauran cututtukan da ban ambata ba. Muna aika maganinmu ko ina tsakanin Nijar da Nigeria, ga masu buƙatar magani da gaske su tuntuɓeni akan lambar wayata 07039080978, ko 09077591726 Noted: *MAI SON MAGANINMU IDAN BA A KADUNA YAKE BA, SHI ZAI YI KUDIN MOTARSA HAR ZUWA INDA YAKE, BABU INDA BAMA TURAWA IN SHA ALLAH.....SAI KUN ZO* 💔💔💔💔❤‍🩹❤‍🩹💔💔💔💔 *DA CIWO A ZUCIYATA* 💔💔💔💔❤‍🩹❤‍🩹💔💔💔💔 _MALLAKIN_ *SAJIDA NIJAR* *FREE BOOK NE* 1️⃣7️⃣ LITATAFAN MARUBUCIYAR Duk karyar kada Yar mahaukaciya Neman na kaina Bani da zabi Bak'a ce Kutkale Makauniya ce Mage Duk nisan jifa Idan ka raina inda kake Dutse Alkalamin kadarata Bani da zabi Dakika Biyar Now *Da CIWO A ZUCIYATA* *Tallah, tallah, tallah* *SECRET DE LA FEMME DU MANGA* _Gidan Kamshi, Sirrin Manyan Mata, nesa tazo kusa,Amarya ,Uwar gida,Ango da mai gida Har ma da yan mata da samari shin kuna sane da cewa HAJIYA FUSAM ta shirya tsaf domin gwangwaje ku da turarakunta masu dankaran kamshi? Tare Kayan gyaram jiki na musamman ,wanda daga nesa kamshin ki kadai ya wadatar ya isar da sakon zuwanki waje,gidan ki kuwa sai ya zam abun kwatance wajen kamshi, kar na cika ku da surutu bara in fara zayyano su_ Farar Humura Bakar Humura Humura special, humura de bain Humura epicé Lait de nuit Parfums désodorisant Parfums rideau et dras Lait de nuit Alkam Kulakcam *Waɗannan kadan ne daga bangaren turaran ruwa* Gagab, sandal flex, Durot, durus, sandal fleur, tafarce, farce, sandal bangui, sandal, hypotonic sandal, al'ut, coktail creation VIP, Gajiji, Mankaji, turaran wutar labule da cafet, Aba malan, boulettes *Munada bangaren gyaran jiki kamar haka:* mai mai saka santsin jiki, mai mai kanshi, Kayan gyaran jiki mai saka fata ta yi santsi da laushi, kayan gyaran jiki mai saka fata ta yi fari, Sabulu mai saka fata ta yi haske, sabulu mai saka fata ta yi santsi, sabulu mai goge yanayin fata, mai wanda baya saka fari mai gyara fata Sayen na gari mai da kudi gida,sai an gwada akan san na kwarai💃💃 Hajiya Fusam na zaune a kasar Niger domin yin magana da ita kai tsaye tuntuɓi wannan number 97 82 44 94 *SECRET DE LA FEMME DU MANGA* Gidan Kamshi, Sirrin Manyan Mata💃💃💃💃💃 Dan juyowa ya yi da alamun a dan kagauce yake ya ce" Hajia ki bani mana ya haka ina ango sai kin sa na je a lati an zane ni?" Dariya maganar ta bata, dan haka ta karaso tana fadin" Ka ga wani sako a wayarka, na san wanda ya turo yana cen yana jiran amsa bai san TAUFEEK NAWA ya turowa sakon ba , ba wani ko inspector ko me ba, inspector fa, kai mu dama mu kurayi numbar a mana hanyar ganninsa ka san wane ake nufi?" Wayar ya cafe dan ya ga number take son fitarwa dan ta yi kira , da yan yatsunsa ya mata alamun ta koma mana, sannan ya tayar da motarsa ya yi tafiyarsa Komawa ta yi tana zumbura baki , hakan ya saka rukaya saka dariya ta ce" Har an bata ko?, Ni kam ina mamakinku, yanzu za'a ga shawara daya yanzu kowa zai kama gabansa" Da haushi ta ce" Ke baya jin magana ne, daga cewa a dauki wata numba a wayarsa a yi kira ya wani warce waya, Allah na tuba da ace banida waya sai na ji haushi, sai me wata wayarsa uwa ta munafukai ba komai a cikinta , kin ga banma fada masa turaransa ya dawo ya amsa gobe ba ya bata min rai" Mama ta girgiza kai tana mamakin itama shirmen Khausar ta ce" To ai goben kwa hadu dole kim manta yace gobe ne zaki fara fita aikin? Kai har gadin abanku nake ya zo da wuri yau ya ga abin arziki, Allah mun gode maka da tarin ni'imomin da ka yi mana, ya rab yadda kake fito mana da hanyoyi ba da tsumi ko dabararmu ba ka nunan auren ya'yan nan lafiya, ubangiji ka sakawa bawan nan naka da ahalinsa da alkhairi, in ba hanya ba ta yaya kai tsaye zamu haka ? Babar asibiti fa, ai kam mu sai yi khausara da allura" Dariya yan matan suka saka dan yadda Mama ta nuna Khausar din zaune an cire hijab za'a sake alwalar sallar isha Rukaya ta ce" Mama, Allah ya sa mabudin dukkan wani alkhairinmu kennan" Mama ta ce" Amen ya hayu ya kayum Rukaya, bi'izinilallah alkhairin kennan" Da wannan suka cika daren ranar, domin da Aba ya dawo tare da auta aka sanar masa alwallah ya daura ya haye darduma ya shiga yiwa ubangiji kirari da fatan Allah ya nuna masa sauranma sun samu alkhairai a rayuwa ya nuna masa aurensu Yauma TAUFEEK ya cika dare sosai, domin ya shantake a wajen abansa ne sun sha hira daga nan kuma ya je wajen Hajia ta gama masa turare turarenta wanda a dole sai da ya je ya yi wanka ya cenza kayansa domin a tunaninsa bangaren Yumnah da baki ba zai je haka yana kauri uwa dan bori ba Yau dinma da hannunsa rike da tsaraba ya karasa bangaren nata Sai dai abin mamaki tunda ya tura ya shiga da salama ya fahimci yau din kamar ita daya ce ba bakinsu Du irin yadda ranta ke bace da gannin rabonsa da ita tunda safe da zasu wuce gaishe da iyayenta da abokansa sai yanzun, ama ganninsa ya saka ranta yin fari, harma ta mike tana murmushi ta nufo shi dan amsar ledar hannunsa Da dan mamaki ya bi shigar jikinta da kallo, riga da wando ne a jikin nata masu tsarin santsi da dan lafewa a jiki kadan, domin idan ka saka su zasu bi tsarin jikinka ne su lafe Dauke kansa ya yi a lokacin da ya tuna cewar ai normal ne yanzu mijinta yake dan an tarbeshi a haka daidai din kennan Yana zama saman kujerar falon yana dan waigawa dan maganar da ya dauka yana fadin" Ina bakin ne? Ko sun kwonta da wuri haka?" Agogo ta kalla bayan ta dauko farin tawul tana dawowa da jug din jus mai sanyi a hannunta ta karaso tana sakin murmushi a ranta ta ayana' Yar banza ce ni zan zauna 8na zubawa karti ido sunna wuni sunna cikan kunne da iya shege bayan ga dalilina a gefe kunya ta hanna shi tarewa da ni?, Bama zai yiwu ba gaskiya ' a bayane kuwa cike da fitar da harufa a tausashe ta ce" Ai dama kwana daidaya ne zasu yi , kusan magariba bayan sun gama girki suka tafi" Murmushi ya yi yana amsar jus din da ta zuba masa ya dan kurba kadan sai kuma ya bita da mamaki gannin ta duba ta kamo kafarsa zata dora saman cinyarta A hankali ya ajiye kofin ya mika hannayensa biyu bayan ya janye kafar tasa yana kallonta da kula sosai ya ce" Hey, yumnah me zaki yi haka ne?" Yumnah ta zubawa fuskarsa ido, cike da tarin kaunarsa ta ce" safar zan cire maka mu je ka yi wanka sai ka ci abinci Yayanmu" Dan murmushi ya yi, kwarai hakan ya birge shi, sai dai a tunaninsa a yanzu shine zai fara riritata, ya bata daraja irin nata, ya nuna mata ita din mace ce, koda zai iya amsar irin kula daga gare ta, dan ba zai tashi zikin kato ya sakata irin wahalar nan ba tana amarya, lada ne ai yanzu suka fara ratabarsa, in sha Allah A hankali bayan ya yi wani yannayi da bata taba ganninsa ya yi ba, yannayi irin na tarin a ji kunyar nan, domin TAUFEEK nata wanda bai cika dogon kallonta bane a yau ya bi rigar jikinta da kallo a hankali ya ce" Na yi wanka ai, sai dai zan so na maki idan Allah ya sa baki yi ba" Ya salam, tabas maganar ta zo mata s ba zata, shi yasa ta wani irin tsare shi da ido cike da mamaki da tunanin shine ya yi furucin nan? Sai kuma wani madaukakin dadi ya nemi rufe dukkan gaban jikinta da yannayinta A hankali ta dan lumshe idannuwanta sakamakon jin hannunsa a saman habarta ya dan murza kadan, baban burinta ta sake ce masa eh tana so ya yi mata wankan, dan irin rayuwar nan ita take hangowa kanta da mijinta dama, su zamto tamkar abu daya komai nasu iri daya Ashe ashe zata iya jin furucin nan daga bakinsa bayan tsoro ya gama mamaye ta cewar wata ta gama yi mata karuwar alaka da miji? Murmushi ya saki , duda a bayane ba zai ce asalin kunya bane ya cinye harshen Yumnah ba, ama daukewar maganarta ya saka shi daukan cewa hakan ne, dan haka ya ringa jin wani sauki sauki a zuciyarsa, domin shi dai da Allah ya halice shi mutun ne mai matukar son mace mai kunya, yana so a rana irin ta yau da wa'inda zasu biyo baya ya zamto ya yaki kunyar amaryarsa , ya koya mata irin yadda ya fi so su kasance cikin koyarwar islama, a duniya ya tsani rawar kai, da shegen banzan yayi irin na wasu matan da mazan, yakan dora laifin haka a kan Mazan ne domin da ace namijin ya nunawa macen yadda zata daidaita lamuranta to da kunya ta zamto ado a motsinta, yana matukar son koda zawara ya aura a yi yayi irin na jin kunyar junna, wasu abubuwan kuwa yau da gobe suke zamtowa dole a saje, ama wasu matan har su mutu akoy yare mai daraja mai sunna kunya a tsakaninsu da mazajensu, dan kuwa du irin sabawar nan da tarin haihuwa wace ke nunin du wani sirri mai sunna sirrinta ya gama sani ciki da bai zaka ga wasu abubuwan a bayane suke na kunya har ana iya gani, shi din da kansa hakan naniya kasancewa nishadi a gareshi, domin yana iya daukan hakan abin tsokanar iyalinsa idan ya yi ta labe fuska ko ta yi shiru ta sada kai, to fa sai ka ga yana dariya a bayane ......., Yana matukar girmama darajar iyayenmu , ba wai gyaran bane ba'a yiwa maza, ba kuma kanshi bane ba'a shaka masu, uwa uba babu wa'inda suka kaisu iya kirsa da sada kai, kai sun fi yan matan iya juya akalar namijin cikin nutsuwa domin su sunna dauke da wani sirri da suka yarda da shi cewa eh a maganar gaskiyama namiji shine shugaba, a kuma maganar hanyar da zasu iya bi su sace zuciyarsama su nuna masa cewar shi din ne dai shugaban, ko magana ta hada su ta rashin fahimta sukan shanye a lokacin su bada hakuri ba dan sun kyale ba, dan kuwa sunna da nasu hanyoyin nuna maka kaime ya dace ka bada hakurin nan fa, harma ka shiga bayarwa ba tare da ka gane hakuri kake bata ba..... Abubuwa ire iren haka dai, shi shine burinsa, shine muradinsa, muhali yake so da rayuwa cike da kula da kare hakoki irin na adininsa da kuma al'adar malan bahaushe, ba rayuwa irin ta turawa ba ............ Da wannan tunanin ya mikar da ita suka karasa wajen diner ya ja mata kujera ta zauna sannan ya ja ya zauna yana dan sakar mata murmushi a lokacin da ta mike tana kokarin zuba masa abincin A nutse ya ce" Kadan zaki saka" Ta kuwa zuba kadan din, sannan ta zuba natama dan kadan sosai, dan ta riga ta ci tun kafin ya shigo, an fada mata cewar kar ta ringa hadama a gabansa Da kula a lokacin da ya fara ci ta ce" Na zata zaka shigo da wuri yau?" Bai bata amsa ba sai da ya gama cin abincinsa a nutse domin dama ba yinwa yake ji ba, ama gudun kar ya shiga hakinta ya saka ya amshi abincin Da kula ya dubeta ya ce" Eh na dan yi wasu uzuririka ne, ama da wuri na shigo daga gidan su KHausar" Cokalin dake hannunta sai da ya kusan fasa plate din da take dan cacaka sanadiyar caka shi da yan yatsunta suka yi da dan karfi Hankali a dan tashe ta ce" Khausar kuma?" A hankali ya dan bi yannayinta da kallo Idannuwanta ta kikifta tana fadin" Me ya jadaka da gidan su KHausar yanzun kuma?, Bayan gani? Ina tunanin a yanzu ai ba Khausar tsohuwar mace ba ko yarinya sabon jinni ce ba zaka kula ba tunda kake da amaryarka a gefe sabuwa fill ko? A tunanina zuwa yanzu ko Khausar ta yi kiranka ba zaka amsata ba tunda gani ko?" Ba da hatsaniya ko ihu ya yi furucinta ba, dan bata taba yi masa magana da ihu haka, tunda ta taba kwatantawa ya nuna mata aa, ba zasu fara haka ba, take kiyayewa, Sai dai ko a hakan a bayane tsagwaron tsanar sunnan wace ta yi magana a kanta ya bayana ba a rufe ba Da mamaki yake kallon fuskarta da ta dauki ja nan da nan A hankali ya kai duban nasa kan hannayenta da take aukin murzawa kamar zata fitar da yan yatsun daga jiki, alamu na a haka din tana dane kanta ainun daga abinda ke zuciyarta Sosai mamaki ya cika masa zuciya Me ya hadata da Khausar mai zafi haka? A sanninsa sunna matukar jituwa tsakaninsu, dan sha nawa zasu samu matsala ita da shi ta samu Khausar din da maganar ita kuma ta ce sai a shirya , ya yi hakuri kuwa su shirya din?, Khausar dai Khausar dinsa ce take nufin a yanzu dan ya aureta du wata alaka zata kunce tsakaninsa da ita? Tana nufin ko wata aka bashi kennan ya mu'amalanta ko mene? Subahanallah shin yarinyar nan bata da wayo ne ko akoy wata a kasa tsakaninta da Khausar? Idannuwansa ya lumshe a hankali yana mai aro nasa yannayi idan ransa ya baci gudun kar ya yi abinda zai iya zuwa ya dawo, watau yin shiru wa abinda ya bata masa ran, rashin tankawa a lokacin har sai ya ji zuciyarsa ta yi sanyi A hankali ya mike da tissu a hannunsa ya wuce ya barta a nan zaune ba tare da ya ce uffan wa maganarta ba A rikice ta juyo ta raka bayansa da kallo har ya bacewa ganninta, sai dai abinda ya dan sanyaya zuciyarta ba waje ya fita ba, aa, ciki ya shige ta hanyar hawa sama A nan a zaune tun tana saka tana warwara har ta ringa gannin kamar ta yi wauta ne ko menene? Kamar ta yi gagawa ne ko menene? Haka kawai zuciyarta ke son nuna mata ta yi azarbabi ita da ya dace ta bi a hankali ta raba wannan banzan tsakanin sai gashi ta yi magana wata iri bayan ta san yana son a ringa tausasa harshe? A hankali ta dafe kanta dake sara mata ta shiga zubar da hawaye msu zafi Shin da wani harshe zata yi kwatance a gane cewar a tsorace take Da wani yare zata yi kwatance a gane irin zafin da take ji a cen kasan zuciyarta? Itace ke wahala, ta fi kowa shiga wani hali a kan mijinta a kan maganar kawarsa Wai kawarsan ce ta kasa yarda cewa kawarsa ce Shin wani abu take bashi wanda ita bata iya bashi ne? Du irin kwaliyarta da zumudinta sai suka dakushe, domin babu abinda ya fi daga mata hankali irin ta ga nasa ran a bace koda wani ne ya bata masa bale ita da kanta Jin kanta zai tsage ya saka ta mike da kyar ta shiga hautawa bata iya koda dauke kayayyakin da suka yi anfani ba, dan so take yi ta je ta same shi ta bashi hakuri Tana shiga ta tarda shi saman salaya , dan haka sai ta nemi waje ta zauna saman gado tana jira ya gama ta bashi hakuri dan bata tunanin ko zata iya dangana ta iya barci da shi haka ba Tun tana tunanin zai gama da wuri har barci ya kwasheta A hankali ya kai dubansa inda take dukunkune ya zuba mata ido, sai kuma ya sauke ajiyar zuciya ya rufe alkur'aninsa ya kai ya ajiye shi a wajen kilacewa sannan ya haura saman gadon yana sake binta da kallo Ya yi haka ne dan baya so yanzu yanzu ta dauko masa maganar Ya yi haka ne dan yana so ya saba mata idan ransa a bace su kiyaye abinda ya bata masan kai tsaye, a bari zukata su huce Dama bashi da niyar tabata a yau, domin ya fi so su saba a hankali kafin ta san shi wanene shima ya san ita wacece Sai dai baya tunanin in har zuciyarsa zata iya lamunce masa sauraronta da murya irin wannan da kalamai ire iren wadinnan Bai san inda abin zai kai iya kaisu ba, gwara su kiyaye A ganninsa idan wani abu ya hadata da Khausar in ba zata iya zumunci da ita ba, to kar ta zageta, dan Khausar a kulun burinta ta faranta mata, ko anguwa suka fita in ta ga abin yan mata sai tace sai an siyawa Yumnah, itace ta koya masa kyautar soyaya ta fada masa a soyaya fa kyauta ake yi ba'a zama ba kyauta dan kyauta itace mai ciyar da soyaya....... Murmushi ya yi ya rufa mata sabon blnkt sannan ya kwonta gefenta kadan bayan ya kashe fitilar dakin *ALLAH BAI SAUKAR DA CIWO BA SAI DA YA SAUKAR DA MAGANINSA* Ni ce dai Fareeda Abdallah, na sake dawo muku da tallen magungunanmu da zuwa yanzu bazan iya ƙayyade yawan waɗanda suka dace da biyan buƙata sanadiyyar amfani da maganinmu ba. Alhamdulillah! Ƴar'uwa ki gwada, wataƙila warakarki na tattare da maganinmu. Haihuwa ce baki taɓa yi ba ko kuwa jinkiri kike samu sanadiyyar planning ko kuma haka kawai? Muna da ingantaccen maganin rashin haihuwa ga mace da namiji, wanda za ki bada sadakar 2k ga matsalar ko wane ɓangare. In sha Allah za ki dawo da godiyarki bayan amfani da maganinmu. Sanyi (infection) ne yayi miki yawa yake saka ki ciwon mara, zubar farin ruwa, ƙaiƙayi, ƙuraje, ɗauke ni'ima, har ma ya saka mijinki ya dinga miki gani-gani saboda bakya gamsar da shi? Da naira 3k zamu haɗa miki magungunan da za kisha ke da Oga in dai kika yi amfani da su ku da sanyi har abada in Allah ya yarda. Muna sayar da ingantaccen haɗin sabaya, wanda zai sa nonuwanki su cicciko, hatta fatar jikinki sai ta murje sanadiyyar shan kunun sabayarmu. 2500 bokiti 1litter. Muna da maganin wankin nono ga mai ciki da mai shayarwa, wanda indai kikai amfani da shi yaronki zaiyi tubarakallah, ba ruwanki da laulayi. Muna da ingantaccen maganin Daji (Cancer), typhoid, maleria, yaron da yayi nauyin ƙafa, da sauran cututtukan da ban ambata ba. Muna aika maganinmu ko ina tsakanin Nijar da Nigeria, ga masu buƙatar magani da gaske su tuntuɓeni akan lambar wayata 07039080978, ko 09077591726 Noted: *MAI SON MAGANINMU IDAN BA A KADUNA YAKE BA, SHI ZAI YI KUDIN MOTARSA HAR ZUWA INDA YAKE, BABU INDA BAMA TURAWA IN SHA ALLAH.....SAI KUN ZO* 💔💔💔💔❤‍🩹❤‍🩹💔💔💔💔 *DA CIWO A ZUCIYATA* 💔💔💔💔❤‍🩹❤‍🩹💔💔💔💔 _MALLAKIN_ *SAJIDA NIJAR* *FREE BOOK NE* 1️⃣8️⃣ LITATAFAN MARUBUCIYAR Duk karyar kada Yar mahaukaciya Neman na kaina Bani da zabi Bak'a ce Kutkale Makauniya ce Mage Duk nisan jifa Idan ka raina inda kake Dutse Alkalamin kadarata Bani da zabi Dakika Biyar Now *Da CIWO A ZUCIYATA* *Tallah, tallah, tallah* *SECRET DE LA FEMME DU MANGA* _Gidan Kamshi, Sirrin Manyan Mata, nesa tazo kusa,Amarya ,Uwar gida,Ango da mai gida Har ma da yan mata da samari shin kuna sane da cewa HAJIYA FUSAM ta shirya tsaf domin gwangwaje ku da turarakunta masu dankaran kamshi? Tare Kayan gyaram jiki na musamman ,wanda daga nesa kamshin ki kadai ya wadatar ya isar da sakon zuwanki waje,gidan ki kuwa sai ya zam abun kwatance wajen kamshi, kar na cika ku da surutu bara in fara zayyano su_ Farar Humura Bakar Humura Humura special, humura de bain Humura epicé Lait de nuit Parfums désodorisant Parfums rideau et dras Lait de nuit Alkam Kulakcam *Waɗannan kadan ne daga bangaren turaran ruwa* Gagab, sandal flex, Durot, durus, sandal fleur, tafarce, farce, sandal bangui, sandal, hypotonic sandal, al'ut, coktail creation VIP, Gajiji, Mankaji, turaran wutar labule da cafet, Aba malan, boulettes *Munada bangaren gyaran jiki kamar haka:* mai mai saka santsin jiki, mai mai kanshi, Kayan gyaran jiki mai saka fata ta yi santsi da laushi, kayan gyaran jiki mai saka fata ta yi fari, Sabulu mai saka fata ta yi haske, sabulu mai saka fata ta yi santsi, sabulu mai goge yanayin fata, mai wanda baya saka fari mai gyara fata Sayen na gari mai da kudi gida,sai an gwada akan san na kwarai💃💃 Hajiya Fusam na zaune a kasar Niger domin yin magana da ita kai tsaye tuntuɓi wannan number 97 82 44 94 *SECRET DE LA FEMME DU MANGA* Gidan Kamshi, Sirrin Manyan Mata💃💃💃💃💃 Koda ta tashi da asubahi bata ganshi a gefenta ba, duda ta ga an rufata sai ta kasa barkata wani abin kirki, a tunaninta baima kwana a cikin gidan ba ya koma inda ya kwana jiya Wannan tunani ya karra saka mata tunanin lalle sai ta yi da gaske, banda hanya irin ta kirsa da zata ara sai ta jajirce ta fadawa Allah ya raba mijinta da wannan fitinaniyar, In ba asiri ta masa ba ta yaya za'a yi a kalli mijinta rikaken namiji mai jini a jika a dangantashi da Khausar?, To ita bata iya bin bokaye ba, ama zata yi dukan abinda ya dace dan gannin ta rana wannan alaka mai wuyar fasara, in Khausar ta iya ruwa bata iya laka ba, da izinin ubangiji zata san tana bibiyar mata miji dan kiri kiri sai ya fi karfinta walahi! Da wannan ta samu ta dira ta yi bayi Ta yi wanka ta kuma dauro alwallah Zuciyarta du bakin kirin na tunanin yau kwana har biyu cif tana matsayin matarsa aman komai bai shiga tsakaninsu ba? Ina ba haka take hango tarayarsu ba, ba haka take hango zamantakewarsu ba Sallah ta yi du rabin hankalinta a waki wajen Tana gamawa bata tsaya yin adu'ar ba ta yi wajen kayan kwaliyarta da sauri ta shiga kimtsa kanta Niyartama tana gamawa ta fice ta yi bangaren manyan ta gaishe su ta yiwu yana cen, inda dai ta san ba zata saka kafarta ba bangaren Hajia ne, dan matar ta tsaneta bata san abinda ta yi mata ba Bayan ta gama kwaliyar ta dauko wata rigarta ta ajiye doguwa ta lesh tana kokarin nemo abinda zata hada mata aka turo kofar aka shigo Da salama ya shigo yana dan shakar kanshin dakin da ta baza na turaren jikinta da ta fesa, sai kuma ya sajke dubansa a kanta a inda take tsaye da doguwar rigar barci da ta saka dan yin sallah da safen Idannuwansa ya dauke a kanta bayan ya ga irin kallon da take binsa da shi idannuwanta na neman kawo ruwa Bakin gadon ya karasa ya zauna a hankali sannan ya sake dubanta a lokacin da ta nufo shi a hankali kamar wata mai jin tsoronsa Yannayinta ya saka shi sasaura fuskarsa sannan ya miko mata hannu A sabauce ta karasa jikinsa ta fada cikin fafadan kirjinsa hannayenta na yin rawa rawa, muryarta na rawa ainun ta ce" Fushi kake yi da ni?, Dan Allah ka yi hakuri, ka yi hakuri ba zan kuma ba, idan na bata maka, ama Yayanmu sai ina jin tsoro, kamar dai baka yi murnar kasancewata matarka ba? Du bana gannin murna a fuskarka" A hankali ya rungumeta bck, idannuwansa a lumshe ya ce" Murna? Yumna ina murna mana, kin san shekaruna nawa ne yanzu? Na fi kowa murnar kasancewarki a rayuwana....." A hankali ta dago tana kallon fuskarsa , hankalinta na sake karantar mata yannayinsa, alamu na farin ciki na son bayana a fuskarta A tausashe sosai ya ce" Shin akoy wani abu da Khausar ta maki kika boye min ne?, Idan akoy shi ki fada min ni zan dauki mataki dan ba zan taba amincewa a wulakanta min ke ko a ci zarafinki ba....." Wani dadi ne ya ringa ratsata, ita? Ashe? Wani irin luuuu ta yi tana kallon fuskarsa, bakinta na nemo laifin da ya dace ace ta fada ama tana ta kai kawo tana tsayuwa a waje daya, laifin da shine kawai take gani kuma shine bata so A tausashe ya ce" Tell me, an yi wani abin da bannsanu bane? Ta maki wani abin da bai dace ba kika boye min ne?" A hankali ta dan girgiza kanta, tana da niyar fadin laifin ya tsatsareta da ido , a tausashe yana dubanta ya ce" Yumnah, kina zargina ne?" Da sauri ta zuba masa ido, ta ce" Zargi kuma?" Idannuwansa ya lumshe matsayin amsa Da sauri ta girgiza kanta ta ce" Ba, bana zarginka, kawai dai ni abotakarku ce nake gannin bai dace ba, ba abota tsakanin mace da namiji, sam bana son tarayarku da ita, daga min hankali take yi, sai in ga ka fi sonta da ni, bayan nice matarka, sai in ga ka fi darajata a kaina" Da mamaki yake kallon fuskarta, wannan din itace hujarta kawai?, Eh lalle a jiya Abansa ke cewa wani sain fa magidanci zaka iya tsintar kanka da rarashi a kan abinda bakama aikata ba, ka yi rarashin dan nima shi nake yi nan da ka gani, ita mace tana iya yin fushi a kan abinda baka taba zato ko tsamani ba, in ka ga hankalinta tashe yi kokari ku sasanta dan sasantawar itace zaman lafiyarka a gidanka "Yumnah, wannan shine dalilinki?" Ya fada yana s9n sake gaskatawa Kai ta gyafa har tana sauke ajiyar zuciya Gefe ya kalla kadan yana ta tunanin to kennan ya shigo fagen da nanata zancen da ya san an sani zai zame masa wajibi? Ikon Allah A tausashensa ya rike hannayenta yana kallonta ya ce" Wannan din, bai dace ya zama abinda zai saka ki bude baki ki yi furuci kamar wace ke zargina da KHausar ba, hakan ba daidai bane sam ba kuma wayo bane, KHausar na santa tun kafin na sanki, a yadda kika ganmu da akoy maganar so da na aureta tun kafin na aureki, ita din tamkar jinnin jikina ce, ina nufin kamar kanaina haka nake dubanta, mu'amalata da ita tsarkakakiya ce, zumuncina da ita mai daraja ne, ina kare mutuncinta dan mai mutunci ce, daga wannan kar ki dada kar ki rage Yumnah, bayan wannan babu wani abu mai iya gigita tunani ko ya saka shaku, na yarda cewa al'adunmu sunna da nasu tafiyar a rashin gannin ire iren haka, hausawa muke, haka adininmu, ama ki yarda tsakanina da KHausar zumunci ne, haka kuma zan iya kare hakinka a gaban kowa...." Ya dan sasaura , a hankali ya dora da fadin" Ke iyalina ce, maganar sonki ko gannin darajarki kin san ya kai matsayin da na aminta har na saka ki dakina......., Ba zan so mu fara takalar magana irin haka ba, zan kuma so li yi zumunci da Khausar idan har kina ra'ayi, in bakya yi ba zan takuraki ba, ama kar ki wulakantata dan ita din a kulun mutuntaki take yi kin fahimta?" Ba ainahin fahimtar ta yi ba, ama a yadda yake zaunen nan ya bata dukkan hankalinsa zata iya cewa rigimar ta lafa a irin wannan lokacin A hankali ta koma jikinsa ta sake makalkale shi hannayenta duka a jikinsa Idannuwansa ya dan lumshe, karfe bakwai ne duka duka na safe, yana fa niyar fitama, haka kuma wannan yannayi yana tsikararsa sosai Kasa kasa ya rada mata maganar da ta sakata dan sake shigewa jikinsa tana sakin murmushi Murmushi ya yi ya sake fadin" ba zaki lafawa tuzurancina bane? Kar fa ki takali dodo ki nemi kumna fitila Yumnah" A ranta fatanta dodon nan ko mai cin dodo ne irinta ta takale shi, burinta itama ta zama matar aure a yau din nan, dan haka cikin dabara, da koyarwar da ta samu ta ringa dan shafa hannunsa zuwa wuyansa kamar da gangan take yi, bayan tana sane sarai, gashi ta idasa cimuymuye rigarsa da Hajia kakarsa ta bashi ta sallah, ta idasa rike shi iya rikewa Tun yana sake tunawa cewar ba yanzu ba, sai da ya tsinci kansa tsamo tsamo a aiki irin na musulmai, aikin da ya zamto gagarumi a gareshi shi kansa, aikin da bai taba kwatanta aikatawa da wata y'a mace a kaf fadin rayuwarsa ba, aikin da yake wuni yana kwana da shi wanda yake tunanin idan ya tashi yi ta yiwu ya karya y'ar mutane, da safiyar gari, da yinwa a cikin y'ar mutane, da komai, haka ya riketa riko na firgici da mamaki, tun tana iya gane sarafa junna suke har ta cenza tunani ta fara tunanin sarafa ake yi, harma ta dawo tunanin ko ranta ake nema? A hankali ta fara bambance aya da tsakuwa, a hankali ta nemi dna juyo da hankalinsa ko zai dakata tun kafin ya fara mai gaba dayan Sai dai sani ne bata yi ba, ba sabon shiga ake yiwa fi'ili ba, ba kuma namiji mai sunna namiji ake tsokana a mike ras kamar yadda aka koyar da ita ba Bata taba tunanin Mijinta ya fi ainahin mijinta girma ba sai da tashin hankalin ya nauje ta ya cakumeta ya nemi karta Wahala iya wahala ta tsinci kanta a ciki a lokacin da summa ta ki zuwar mata take farke tana sauraron aikin likita Jigatar shima ya jigata dan yau ya fara sauke nauyin nan kuma a irin lokacin nan da ya dan warci furana wajen hajia cikinsa ya dan dauka kadan Da wannan suka sasaba har Amarya Yumnah ta samu abinda take nema, sai dai wa ya sani tana kan bakanta na mikewa ta kabe ta kile ?......... (😂 han) _______________________________ Karfe bakwai na safe ta shirya , shiryawa mai tsafta da tsari daidai da kwaliyarta Hijab dinta na sallah sabo fil fari kal ta saka sannan ta saka takalmin auren TAUFEEK ta aniya kai kawo sai sakin murmushi take yi Zazafe da aka zubo ta karewa kallo ta cire kai tana murza dari biyar din da Aba ya wanka mata mari da ita da asubahin Allah, ita ta san yau zata shiga cikin tarihin rayuwarta domin zata ci kwan kifi iya ci a kofar asibiti sannan ta ci dambun nan na kofar asibiti mai dadin balaki, ita kam yau me zai hadata da zazafen Mama? Aa gaskiya, to mema ya hada likitama da zazafe fisabililahi? Sintirin da take yi yan uwan ke bi da kallo har Mama ta fito daga gyaran dakin abansu domin ita ke gyaran abinta har yanzun bata barwa yayanta wannan ba, ta mikawa Khausar sharar ta kai ta zubar ta dawo ta yi wani kikam ta ki zama sam sai aukin duba agogon da ta daura a hannunta take yi baka yar siririya tun ta sallarsu ta bara da Aba ya siya masu Mama dake zama saman tabarma ta janyo kwanon abincinta ta sake kallon KHausar ta ce" Ke wai ya hala, ki nemi waje ki zauna mana, ya baki karya ba kuma?" Khausar ta kalli abincin ta girgiza kai a hankali ta ce" Mama ai yau ba zan ci tuwon laushi ba, kin ga dari biyar Aba ya bani, kuma shiry TAUFEEK din bai zo ba har yanzu kar fa na yi lati, Aisha ke dan bani wayarki na yi kiransa?" Mama da mamaki take kallonta ta ce" Ke zo nan zauna" Khausar ta karaso inda Mama ta nuna mata ta zauna tana kallon maman gannin ta sha kunu Mama ta ce" Dari biyar din duka zaki je ki juyewa ciki sai kace baiwar ciki? Bayan ga abinci a gida? Karma mu fara haka da ke maza ki cire dari biyi ki saka a cikin asusunki, sannan maganar TAUFEEK, Khausar zuwa yanzu fa sai kin kiyaye wasu abubuwan, kamar su yawan kiranshi, kiranshi kowani lokaci, ke harta yawan ganninki tare da shi, dan kin ga yanzun sunnansa mai mace, ba daya bane da da, ita zuciya bata da kashi matarsa na iya jin ba dadi, kuma tana da gaskiya dan ko ba komai hausawa muke ai ba yaren yahudu ba, ke kin san yaya aka yi muka yarda da tarenku sai da muka yarda cewa eh ta zumunci ce, ama duda haka ba wani sakankancewa muka yi da ku ba, dan haka ba zamu yarda yanzu tarenku ya hadasa fitina da matarsa kin gane?" Khausar kallon Mama take yi da mamaki Ta rage kiran TAUFEEK? Ta rage karfin mu'amalarsu dan ya yi aure? To ita me hadinta da aurensa? Ita ai itacema zata gyara aurensa ba ta hada rikici ba, ama irin yadda Mama ta daure fuska a dole ta amsa da to ta kuma kai dari biyu ta saka a asusu sai cika kunci take ta zo ta zauna ta shiga shakar zazafe bayan ita ta san cewa ba girman likitoci bane daukan tuwo da safiyar gari ( ki rufawa kanki asiri autar Aba, ki ci ki yi nak, aikin asibiti ba'a yi da yinwa bale din nan kar ki je ki baje kina hailala😌) Wasa wasa sai da ta ba karfe goma sha daya baya na rana tana jiran tsamani, ta ki ko hijab din ta cire a zaunen da take, dan shi yace za'a kaita kar ta je kai tsaye, gashi Mama ta yada dokar kar ta saki ta ringa kiransa yanzun, sai kawai ta ji kamar ta yi ta ihu a zaune Sai kusan sha biyu aka yi salama aka sanar da ita direba ne daga gidan mai kwanoni ta fito a kaita asibiti Har gudu gudu take yi wajen saka takalma Mama na yi mata addu'a har ta shige motar tana tambayar ko TAUFEEK ya yi tafia ne? Shi dai direban bai san amsar bata ba ya dai kaita har inda akace ya kaita sannan ya juya A darare take kale kale a baban filin bangaren Emergency, bata san inda zata nufa ba, bata taba tunanin zata iya tsintar kanta da tsoro da shayi ba sai a yau, kallon mutanen dake kai kawo yake yi zuciyarta cike da tunanin me ya hannata dauko wayarta ne? Tunda suka yi waya da Elhaji jiya ta kashe wayar bata kunnata ba dan yace shi zai kawota asibitin yau, ita kuma bata son takura Ajiyar zuciya ta sauke ta nufi hanyar shiga emgncy din Mutumen dake gadin wajen yana tsaye kikam fuskar nan ba annuri ne ya sakata dakatawa tana kallonsa da tunanin anyama bahaushe ne? So ta yi ta rabe ta shige salim alim, ama kuma ta san waye shi, dan ko kana zuwa dubiya ka san su waye masu tsaron kofofin asibitin, basa sasauci dan bada tsaro a hanyar Murya na rawa ta ce" Ina yini Baba" Kallonta ya yi kallo daya sannan ya dauke kai, wai Baba? Shi baban da tace masa ne ya bata masa raima ba kallon kure muninsa da ta tsaya yi ba Shi bai ce mata Mama ba dan tsohon raini zata wani ce masa Baba? Takardar ta fitar tana dan matsowa ta ce" Ka ga yau akace na zo na fara aiki, ga takardar nan" Yanzun kam a wawure ya wawura mata kallon ta mutu ta lalace, aiki? To ko mau mukami ce dai? Ko babar docter ce ai ba haka ake zuwa ba, bale ta yiwu karamar likita ce, ta rasa lokacin zuwa sai yanzu? Lalle tana da tashin hankali a gabanta bale yau gidan a dinke yake da dakarun masu saita ire irensu Hanya ya bata ta shiga ko ci kanki bai ce mata ba, ya san za'a rama masa kiransa baba da ta yi in dai ta shigan, ba sai ya rama da kansa ba gaskiya 😂😂😂😂😂😂😂😂 Wayo mu, Khausara Allah ya bada Sa'a yar gidan Aba *ALLAH BAI SAUKAR DA CIWO BA SAI DA YA SAUKAR DA MAGANINSA* Ni ce dai Fareeda Abdallah, na sake dawo muku da tallen magungunanmu da zuwa yanzu bazan iya ƙayyade yawan waɗanda suka dace da biyan buƙata sanadiyyar amfani da maganinmu ba. Alhamdulillah! Ƴar'uwa ki gwada, wataƙila warakarki na tattare da maganinmu. Haihuwa ce baki taɓa yi ba ko kuwa jinkiri kike samu sanadiyyar planning ko kuma haka kawai? Muna da ingantaccen maganin rashin haihuwa ga mace da namiji, wanda za ki bada sadakar 2k ga matsalar ko wane ɓangare. In sha Allah za ki dawo da godiyarki bayan amfani da maganinmu. Sanyi (infection) ne yayi miki yawa yake saka ki ciwon mara, zubar farin ruwa, ƙaiƙayi, ƙuraje, ɗauke ni'ima, har ma ya saka mijinki ya dinga miki gani-gani saboda bakya gamsar da shi? Da naira 3k zamu haɗa miki magungunan da za kisha ke da Oga in dai kika yi amfani da su ku da sanyi har abada in Allah ya yarda. Muna sayar da ingantaccen haɗin sabaya, wanda zai sa nonuwanki su cicciko, hatta fatar jikinki sai ta murje sanadiyyar shan kunun sabayarmu. 2500 bokiti 1litter. Muna da maganin wankin nono ga mai ciki da mai shayarwa, wanda indai kikai amfani da shi yaronki zaiyi tubarakallah, ba ruwanki da laulayi. Muna da ingantaccen maganin Daji (Cancer), typhoid, maleria, yaron da yayi nauyin ƙafa, da sauran cututtukan da ban ambata ba. Muna aika maganinmu ko ina tsakanin Nijar da Nigeria, ga masu buƙatar magani da gaske su tuntuɓeni akan lambar wayata 07039080978, ko 09077591726 Noted: *MAI SON MAGANINMU IDAN BA A KADUNA YAKE BA, SHI ZAI YI KUDIN MOTARSA HAR ZUWA INDA YAKE, BABU INDA BAMA TURAWA IN SHA ALLAH.....SAI KUN ZO* 💔💔💔💔❤‍🩹❤‍🩹💔💔💔💔 *DA CIWO A ZUCIYATA* 💔💔💔💔❤‍🩹❤‍🩹💔💔💔💔 _MALLAKIN_ *SAJIDA NIJAR* *FREE BOOK NE* 1️⃣9️⃣ LITATAFAN MARUBUCIYAR Duk karyar kada Yar mahaukaciya Neman na kaina Bani da zabi Bak'a ce Kutkale Makauniya ce Mage Duk nisan jifa Idan ka raina inda kake Dutse Alkalamin kadarata Bani da zabi Dakika Biyar Now *Da CIWO A ZUCIYATA* *Tallah, tallah, tallah* *SECRET DE LA FEMME DU MANGA* _Gidan Kamshi, Sirrin Manyan Mata, nesa tazo kusa,Amarya ,Uwar gida,Ango da mai gida Har ma da yan mata da samari shin kuna sane da cewa HAJIYA FUSAM ta shirya tsaf domin gwangwaje ku da turarakunta masu dankaran kamshi? Tare Kayan gyaram jiki na musamman ,wanda daga nesa kamshin ki kadai ya wadatar ya isar da sakon zuwanki waje,gidan ki kuwa sai ya zam abun kwatance wajen kamshi, kar na cika ku da surutu bara in fara zayyano su_ Farar Humura Bakar Humura Humura special, humura de bain Humura epicé Lait de nuit Parfums désodorisant Parfums rideau et dras Lait de nuit Alkam Kulakcam *Waɗannan kadan ne daga bangaren turaran ruwa* Gagab, sandal flex, Durot, durus, sandal fleur, tafarce, farce, sandal bangui, sandal, hypotonic sandal, al'ut, coktail creation VIP, Gajiji, Mankaji, turaran wutar labule da cafet, Aba malan, boulettes *Munada bangaren gyaran jiki kamar haka:* mai mai saka santsin jiki, mai mai kanshi, Kayan gyaran jiki mai saka fata ta yi santsi da laushi, kayan gyaran jiki mai saka fata ta yi fari, Sabulu mai saka fata ta yi haske, sabulu mai saka fata ta yi santsi, sabulu mai goge yanayin fata, mai wanda baya saka fari mai gyara fata Sayen na gari mai da kudi gida,sai an gwada akan san na kwarai💃💃 Hajiya Fusam na zaune a kasar Niger domin yin magana da ita kai tsaye tuntuɓi wannan number 97 82 44 94 *SECRET DE LA FEMME DU MANGA* Gidan Kamshi, Sirrin Manyan Mata💃💃💃💃💃 Jiki du ba karfi ta shiga A hankali take tafia idannuwanta na sauka kan abubuwa kala kala, kama daga mararsa lafiya daidaiku a zaune a layi, masu jinya daidaiku haka, sai likitocin dake ta shige da fice dakunna kowane kamar ana biye da shi da gudu ga dukkan alamu aiyuka suke kaan yi ba kama hannun yaro A tsorace ta juya wajen da kunnanta ya amsa amon magana kamar haka" waye a bakin hanya ne? Waye a tsaye bakin hanyar zuwa Morgue?" A rikice ta kauce kamar yadda wata mata likita ta ja hijabinta gefe da dan alamun fada ta ce" Ke ya haka kina gani za'a wuce kin tare hanya? Wa kike jinya ne kika tsaya mana a bakin hanya?" KHausar du sai abin ya zo mata a hade a hade Hannunta na rawa tana mikawa matar ambulop din da akace in ta zo ta bada idannuwanta suka sauka a kan gado mai tayoyin da aka turo dauke da mutun sama ama an rufe shi har kansa da abin rufa, wanda ke tura gadon hannayensa da safa, sai mutane biyu dake biye da gadon sunna kuka , hakan ya mata nuni cewar gawa ce aka wuce da ita nan da nan daga shigowarta Wani irin sarawa kanta ya yi a lokacin da matar ta wafci abin hannunta tana fadin" Ko dai likitar kurame aka turaki kika zo nan ana magana kin mana shiru?" Jiki a matukar sanyaye khausar ta so cewa aa, sai dai kafin ta yi magana ta ga matar ta dago da mamaki ta bita da kallo tun daga kafarta har zuwa dandar kanta Bata yi magana ba sai kai da ta gyada da hannu ta mata alamun ta biyota Binta take yi jiki du a sabule suka nufi wani office da ga dukkan alamu office sin baban wajen ne gana daya wanda ke kula da wajen gaba daya Bubugawa matar ta yi sannan ta juyo ta sake zubawa Khausar ido, hakan ya sa du ta tsargu ta sada kai tana ta addu'a a ranta, abinda ya fi rikitata gawar cen, ba wai dan bata taba gani ba, sun je kauye ai koyon aiki na wata uku uku, ama gawar har suka yi suka gama biyu aka yi rasuwar itama ta zo an tafi da gawar ne Gannin matar ta shiga ya saka ta bi bayanta sannan ta ja ta tsaya daga dokin kofar tana sake sada kanta Karasawa matar ta yi bayan ta gaishe da likitan dake zaune yana ta aiyukansa sannan ta mika masa takardar dake hannunta "Hajia rauda idan kin san aiki kika kawo min kima juya da abinki" ya fada yana duba takardar Yar dariya ta yi ta ce" Wane ni docter, bakuwar wajen oga ce" Da sauri ya dago dan son gannin inda bakuwar take, wace ya yi tsamaninta dunda sanyin safiya harma yake zaune har zuwa yanzu a asibitin saboda ita bayan aikin dake gabansa Shima kallon da Hajia Rauda ta mata ya mata, sannan ya kalli Hajia Raudar da dan mamaki, sai kuma ya cire kansa Kasancewar dazu kasa kasa suke yin magana, yanzunma sai ya mata kasa kasan ya ce" Yaya zamu yi kennan? Zuwanta nan a wannan lokacin zata take abinta ne dan tana bakuwa daga oga?" Hajia Rauda ta girgiza kai ta ce" Ai ka san ba haka, kuma shi ya koya haka, ba maganar ta gida a aikin asibiti, so hukunci ya hau kanta kawai " Kai ya gyada ya nuna mata rigunnan da aka warewa Khausar din, da safar hannu da takalmi kwaya biyu sannan ya ajiye takardun a nan saman table din ya ci gaba da aikinsa Rigar daya ta bude ta mikowa Kausar tana fadin" Maza cire hijabin nan ki saka rigar ga takalmin mu je" Kausar ta amsa da hannu biyu gabanta na faduwa , ta cire hijabin? Da sauri ta debe hijabin cikin gagawa ta saka rigar fara kar budadiya sosai wace ta kusan yi mata daidai ama wajen cinyoyinta sai ta dage sosai Cikin sauri ta saka takalmin sannan ta saka safar hannun tana sake gyara hular dake kanta a cikin zuciyarta tana tunanin lalle akoy aiki a gabanta Hijab din ta dauko da niyar mayarwa Hajia Rauda ta kalleta da mamaki ta ce" Kina ji? Abubuwan da zan fada maki su zamto na farko na kuma karshe da zamu tatauna a kansu Na farko ga takarda da zaki cike ta bayanin dalilin da ya saka kika zo a lati , na biyu wannan zane zane na hannayenki ba naki bane yanzu dan aiki kika zo koya, na uku hijabin irin wannan ba na aikinki bane, idan kin zo ki tabata kin saka dan karamin hijab wanda ba zai hannaki aiki ba, sai kula da dukan aikin da aka baki a kan lokaci kin fahimta?" Kai take gyadawa da sauri tama rasa me zata ce Matar ta karbe hijabin suka fito daga Khausar sai hular nan suka nufi wani office din Nan Allah ya taimaketa matar ta bata baby hijab , tana sakawa ta kuma janyota suka nufi wani dakin da yar hayaniya ta yi yawa Sunna zuwa suka tarar da abinda Khausar ke iya kira tashin hankali, domin accident ne aka yi du an shanshanya mutane Sai dai abin rikicewar zuciyar shine wanin ya samu karaya ne kashi a fili, wanin a inda yake jini ne ya bata wajen , uwa uba wanda ya samu kunna a barin jikinsa Tsintsiya da abin gugar da aka miko mata aka nuna mata wajen mai kunnar dake yashe shima ana duduba shi cewar maza ta je ta kimtsa wajen dan ya bata shi ta rike jikinta na rawa hancinta na jin karnin jinni, idannuwanta na kallon jinni da ciwo, tun tana iya jurewa wajen wanke gadon har abin ya kai wuyanta ta shiga sheka amai tamkar zata amayar da hanjin cikinta, sai dai abin mamaki masu jinyar mararsa lafiya kawai suka iya nuna mata kamar sun damu, babar likitar nan aiki take ba kama hannun yaro ana ta raraba mararsa lafiyar har sai da ya zamto ba kowa a dakin na farko ta juyo kanta ta kama kafadunta ta mikar da ita tsaye tana kallonta cikin ido ta ce" Sai fa kin kama jikinki, sai kin wanke idannuwanki, dan inda aka kawoki ana kaunarki aka kawoki, domin nan ba zaki fita ba sai kin goge iya gogewa a aiki, ama fa kin ga rama? Sai kin rame, sai hankalinki ya tashi, domin wani abin idan kika gani zaki sha kuka kamar ranki zai fita, ki jure kawai , ki jure kawai haka aikinki ya gada, ki gama wanke jinin nan tas, ki shiga dakunan cen biyu summa ki wanke sosai su fita sai ki zo cen wajen office din Samira ki tsaya ki yi pansema" Daga haka ta wuce ta bar Khausar daga ita sai ita a dakin nan Ido du a waje hankali a tashe Du yadda ta hasasowa kanta tana iya haduwa da tashin hankali abin ya zarce haka, tun tana gane yannayin lokaci har ya shige mata ta daina fahimtar dare ya yi ko har yanzu a cikin wunin ranar ake Juwa ke dibanta du idan ta motsa ama ta gaza zama bale ta kwonta Yinwa take ji tun bayan yin amanta, ama a hankali yinwar ta disashe ta daina jinta Idan ta ga an nufi sallah sai ta je ta yi a irgenta sun gabatar da sallar isha ama shiru ba'a salameta ba Ido ya gama yi mata zuru zuru ya mutu murus kwalin da ta saka du ya jeme da kukan da ta yi Tun tana tunanin ranar zata kare ta tafi ko ta daina irga gawa har ta dawo idan ta ga an rufe sai ta yiwa mamacin addu'a a zuciyarta, ama idannuwanta sun gaza daina kuka Tana tsaye, kaffafuwanta sun sage, tana tare da wasu likitocin da take masu kallon kamar wa'inda basa jin komai a gaban jikinsu kamar ba mutane ba? Sunna kai kawonsu ba alamun gajiya a tatare da su tamkar su din basa jin gabai na jikinsu Ita dai bata ga lokacin da suka tsaya cin abinci ba, dama dama dazun da 5a shiga sake wanke fuskarta ta ga wani namiji a tsaye yana tura wani abin a bakinsa ama bata san abinci ne ko menene ba A yanzun da suke tsayen ta gama yankewa cewar a yau fa ta yiwu karshenta kennan kanta a kasa ta ji Hajia Rauda na magana cewar ta dauko hijabinta ta tafi gida, kar ta manta gobe karfe takwas na safe ya mata a nan idan ba haka ba zata hadu da punichment mai tsauri, sannan ta tafi da takardar rubuta dalilin yin latinta yau Bata taba tsamanin idan akace Khausar jeki gida zata ji kamar ance Khausar shiga aljannah bane sai yau Wani irin salama da zazabin dadi ya sauka a zuciyarta Irin yadda take sauri ta nufi office din ta dauko baban hijabinta ta saka a saman kayan aikin ko takalminta bata tuna ba bale ta cire rigar da aka bata ta saka ta yi aikin Salama ta masu ta fice tana tunanin ai bama zasu kuma ganninta ba bale su kasheta, Hajia Rauda kuwa ta yi murmushi a ranta ta yana' Ta yiwu da gangan chef ya turoki a lati dan ya ga yadda zamu maki, na tabata in kika fada masa zai yarda cewa muna aikinmu ba shiririta muke yi ba' Da sauri ta fito daga Emrgncy din ita kadai sai shasheka take ta shiga tunanin abin hawa Idonta idon mai tsaron kofar nan sai ta ga kamar wanda ya yi murmushi, tuna cewar murmushin me zai yi ya sakata dauke kanta a ranta tana tunanin yinwar da ta fara tuna mata cewar akoyta fa ce ta fara sakata gani gani a hanya Ta fara tafiyawa kennan wata watsetsiyar mota ta parker gabanta kadan Niyarta ta dan dakata motar ta wuce sai ta nemi abin hawa sai gannin Aisha ta yi ta fito daga motar tanna yar dariya hadi da fadin" Likita bokan turai, Aunty an fito?" KHausar ta dan zuba mata ido, ta kifta a hankali tana kallonta , murya a raunane ta ce" Aisha kece?" Aisha ta yi mata wani kallo jin tana tambayarta ko itace, sai kuma ta kamo hannunta ta janyota tana fadin" Zo mu je, yaya TAUFEEK ne ya zo daukarki, tun dazun Baba ya kasa hakuri ya tabo shi, shine ya je ya kwatantawa Baba yanzun fa sai an yi hakuri dole an jure , wai harda gadi zakina yi akace ko me? Kingama sai da muka biya butique din nan baba muka siyo maki hijabai masu yawa walahi wai a saman rigar aiki ake sakawa inji shi" Bude mata gaba ta yi tana mata alamun ta shiga mana, Khausar ta bude baki murya na rawa ta ce" Aisha yinwa nake ji" sai ga hawaye sharrrrr sun fara bin kumatunta A hankali TAUFEEK ya labe fuskarsa yana sakin murmushi Aisha kuwa da mamaki ta ce" Kai aunty, dari uku fa kika zo da ita ai ya ci ace ta isheki , Mama fa ta ajiye maki doyarki " Khausar ta samu ta shiga motar da kyar tana share hawayenta ta ce" Ni nama manta da kudin nan, kin ga abin hawa ne fa nake nema idan na je Aba ya biya, ba zan iya wannan aikin ba, a yau wankin jinni na ringa yi da gadajen da aka rasu, Aisha rasuwa biyar aka yi a gabana ana rufewa ana fita da su, Aisha an yi karaya kashi a fili aka hade aka dinke ina kallo, tunda na shiga ban zauna ba a tsaye nake, ko ruwa ban sha ba babu wanda ya bani, ki duba ki ga yadda jikina ke rawa, idan na yi sati a wajen nan ni na san ramar da zan yi ko mai cutar s wanda baya daukan magani sai ya fini kyan jiki, walahi TAUFEEK ba zan iya ba, sai in mutu, kamar wanda suke jirana? Kamar wace na masu laifi, wai dan na zo a lati ka ga harda takardar na cike dalilin zuwana a lati bayan ba laifina bane, TAUFEEK ba zaka taba iya aikin Asibiti ba, na rantse maka sai ka summa kai da baka son wahala ko ta rana ce bale irin wannan, TAUFEEK gawa gawa kamar me, ashe haka ake mutuwa? Kai da baka saba ba ai na san bama zaka iya ba" Da kyar ya iya hanna kansa dariya, bale da take hawaye ka'in da na'in Ceinduith din da ya siyo ya juya ya dauko ya miko mata da ruwa ama ba masu sanyi ba masu dumi dumi yana gimshewa kadan ya ce" Amshi dan fara shan ruwan kadan sai ki ci" Ruwan ta dan rike, jin bashi da sanyi ta dube shi fuska har yanzu a raunane ta ce" Besty, ruwan ba mai dan sanyi sanyi?" Kai ya gyada mata sannan ya tayar da motar dan karma tace zata sayi mai sanyin , a irin yadda cikinta ya shaki abubuwan da bata taba shaka ba in ta fara shan ruwa mai sanyi da yawa zata sha, in kuwa ta sha da yawa cikin zai kule ne ya kama ciwo Haka ta ringa tura abincin nan kafin su karasa gida Sunna zuwa ya dubeta fuskarsa ba alamar dariya ya ce" Gobe, idan Allah ya kaimu ki shirya da wuri ki tafi a kafa, jikinki zai saba ne da wahalar , ba maganar wai kin daina zuwa kin fahimta" Da mamaki take kallonsa, shi dan bai ji abinda ta ji bane, koda yake dama haka zai ce mana shi da shine ta tabbata bama zai iya tsayuwar minti ashirin ba , tsafma zai ajiye karatun asibitin tunda dama su suke so ya yi ba shi yake so ba Motar ya kunna yana sake dan haske ta Mujahid dake parker ya mata alamun ta fita mana Fita ta yi tana turo baki ta yi baya kadan har ya tayar ya yi gaba Harga Allah bata gane motar waye gaba da gidan kadan ba sai da ta tsinci murya kasa kasa da tsayinta haka ana fadin" Watau Motatace ba zaki shiga ba sai ta Elhaji TAUFEEK? Khausar wannan kawance da Elhaji TAUFEEK zan iya rabashi kuwa? Ina nufin idan kika zama matata kin san ai ko magana haramta maki zan yi da shi tunda ba muharaminki bane!" Da zafi zafi yake maganar, har kamarma yana huci gaskiya Da farko tsoratama ta yi, sai da hasken farin wata ya dale mata sankonsa ta yarda cewa shine Dan rage tsayinta ta yi tana gaisar da shi, da kula sosai da mutuntawa ta ce" Yah Mujaheed barka da warhaka, ban san zaka zo yau ba ai" Baki ya dan tabe cike da kishi ya ce" Yaya zaki yi ki sani kin kashen waya ama k8n kunnawa Elhaji, Khausar gwarama ki ba maganata mahinmanci , ko dai ke din ba matar karamin mutun irina bace?" Mamaki madaukaki ya kamata, wai me yake damun bawan Allahn nan ne yau? Ji fa wasu magangannu kuma fisabililahi, me yake faruwa da shi ne haka?, Gajiyar dake tare da ita kadai ta isheta, kanta ciwo yake yi haka gaban jikinta, dan haka a tausashe ta dan sake risinawa dan bata son tana saman nan yana kasa walahi, ta fi so ta ringa rage tsayinta sosai in dai zasu yi magana ta ce" *ALLAH BAI SAUKAR DA CIWO BA SAI DA YA SAUKAR DA MAGANINSA* Ni ce dai Fareeda Abdallah, na sake dawo muku da tallen magungunanmu da zuwa yanzu bazan iya ƙayyade yawan waɗanda suka dace da biyan buƙata sanadiyyar amfani da maganinmu ba. Alhamdulillah! Ƴar'uwa ki gwada, wataƙila warakarki na tattare da maganinmu. Haihuwa ce baki taɓa yi ba ko kuwa jinkiri kike samu sanadiyyar planning ko kuma haka kawai? Muna da ingantaccen maganin rashin haihuwa ga mace da namiji, wanda za ki bada sadakar 2k ga matsalar ko wane ɓangare. In sha Allah za ki dawo da godiyarki bayan amfani da maganinmu. Sanyi (infection) ne yayi miki yawa yake saka ki ciwon mara, zubar farin ruwa, ƙaiƙayi, ƙuraje, ɗauke ni'ima, har ma ya saka mijinki ya dinga miki gani-gani saboda bakya gamsar da shi? Da naira 3k zamu haɗa miki magungunan da za kisha ke da Oga in dai kika yi amfani da su ku da sanyi har abada in Allah ya yarda. Muna sayar da ingantaccen haɗin sabaya, wanda zai sa nonuwanki su cicciko, hatta fatar jikinki sai ta murje sanadiyyar shan kunun sabayarmu. 2500 bokiti 1litter. Muna da maganin wankin nono ga mai ciki da mai shayarwa, wanda indai kikai amfani da shi yaronki zaiyi tubarakallah, ba ruwanki da laulayi. Muna da ingantaccen maganin Daji (Cancer), typhoid, maleria, yaron da yayi nauyin ƙafa, da sauran cututtukan da ban ambata ba. Muna aika maganinmu ko ina tsakanin Nijar da Nigeria, ga masu buƙatar magani da gaske su tuntuɓeni akan lambar wayata 07039080978, ko 09077591726 Noted: *MAI SON MAGANINMU IDAN BA A KADUNA YAKE BA, SHI ZAI YI KUDIN MOTARSA HAR ZUWA INDA YAKE, BABU INDA BAMA TURAWA IN SHA ALLAH.....SAI KUN ZO* 💔💔💔💔❤‍🩹❤‍🩹💔💔💔💔 *DA CIWO A ZUCIYATA* 💔💔💔💔❤‍🩹❤‍🩹💔💔💔💔 _MALLAKIN_ *SAJIDA NIJAR* *FREE BOOK NE* 2️⃣0️⃣ LITATAFAN MARUBUCIYAR Duk karyar kada Yar mahaukaciya Neman na kaina Bani da zabi Bak'a ce Kutkale Makauniya ce Mage Duk nisan jifa Idan ka raina inda kake Dutse Alkalamin kadarata Bani da zabi Dakika Biyar Now *Da CIWO A ZUCIYATA* *Tallah, tallah, tallah* *SECRET DE LA FEMME DU MANGA* _Gidan Kamshi, Sirrin Manyan Mata, nesa tazo kusa,Amarya ,Uwar gida,Ango da mai gida Har ma da yan mata da samari shin kuna sane da cewa HAJIYA FUSAM ta shirya tsaf domin gwangwaje ku da turarakunta masu dankaran kamshi? Tare Kayan gyaram jiki na musamman ,wanda daga nesa kamshin ki kadai ya wadatar ya isar da sakon zuwanki waje,gidan ki kuwa sai ya zam abun kwatance wajen kamshi, kar na cika ku da surutu bara in fara zayyano su_ Farar Humura Bakar Humura Humura special, humura de bain Humura epicé Lait de nuit Parfums désodorisant Parfums rideau et dras Lait de nuit Alkam Kulakcam *Waɗannan kadan ne daga bangaren turaran ruwa* Gagab, sandal flex, Durot, durus, sandal fleur, tafarce, farce, sandal bangui, sandal, hypotonic sandal, al'ut, coktail creation VIP, Gajiji, Mankaji, turaran wutar labule da cafet, Aba malan, boulettes *Munada bangaren gyaran jiki kamar haka:* mai mai saka santsin jiki, mai mai kanshi, Kayan gyaran jiki mai saka fata ta yi santsi da laushi, kayan gyaran jiki mai saka fata ta yi fari, Sabulu mai saka fata ta yi haske, sabulu mai saka fata ta yi santsi, sabulu mai goge yanayin fata, mai wanda baya saka fari mai gyara fata Sayen na gari mai da kudi gida,sai an gwada akan san na kwarai💃💃 Hajiya Fusam na zaune a kasar Niger domin yin magana da ita kai tsaye tuntuɓi wannan number 97 82 44 94 *SECRET DE LA FEMME DU MANGA* Gidan Kamshi, Sirrin Manyan Mata💃💃💃💃💃 A sanyaye sosai ta ce" Dan Allah ka yi hakuri Elhaji, a nan ban ga abin bacin rai ba sam, wayana tana gida yau tunda na tafi wajen aiki ban zauna ba sai yanzu da Aba ya saka ya daukoni, TAUFEEK fa dan uwana ne ba wani abu da zai taba shiga tsakanina da shi, dan Allah kar hakan ya saka ka fara wasu tunani a kan zumuncina da shi, domin shi din ya min halaci kuma yana cikin yi min " Maimakun sanyayawarta, tausasawarta, da kalamanta naa fahimta su dan ganar da shi inda ta nufa sau ya ga ta karra rufa TAUFEEK, to in bama wulakanci ba shi zata duba tace wai TAUFEEK dan uwantane? Na ina? Tare numfashinta ya yi ya ce" Ba sai kin nunan kin gaji kina son shiga gida ba, dama kulun a gubdure kike in ina gefenki, ki sani dan ya fini kudi ba yana nufin zai iya yin kyauta fiye da tawa ba, ko a gari ni an sanni in ina neman aure har gida bake ba budurwar, kema kun katsenine tun farko domin da kun barni da yanzu ba haka kike yawo ba sai a motar kanki, kuma da na cireku a gidan nan na maida ku wanda ya fi shi, nima ina iya yi maki halaci sosai Khausar dan ina sonki, bara na tafi na barki ki huta idan na dawo ma yi maganar, ki yi tunani sosai a kan maganata ta Elhaji, ni kam bana son tarayarku!" Da ido ta raka shi har ya bacewa ganninta Zuciyarta ta ji ta sake cinkushewa sosai har kamar zata kifa daga tsayen da take Da kyar ta lalubi gidan ta shige da salama kasa kasa, Idannuwanta suka sauka a fuskar Aba dake sake fadada fuskarsa da murmushi yana fadin" Oyoyo ga bokan turaina, ga autana, ga shalelena, ga masu yaki da allurana nan" A hankali ta ja numfashi tana kallon fara'ar dake kan fuskar mahaifinta, a sanyaye ta shagwabe fuskarta ta sake kifta ido, sai ga abinda ba zata iya rikewa a gabansa, da mama, da TAUFEEK ba, watau hawaye, Mama dake lekenta ta koma tana dariya dan ta san in ta fito abin kamari zai yi har ta mangareta, domin Aisha ta fada masu a dane take , a sama take sosai har tace wai ba zata koma ba, shi yasa Abansu ya kori kowa ya shinfida tabarma da ruwa da abincinta dan ya san in ta dan fara jajen dole a bukaci ruwa dan a dan jika makoshi a kuma ci abinci dan a sake samun karfi kadan, fatansa dai ta sauka da wuri dan ya fita ya siyo nata panadol ta dan hadiya, ko jikin ya dan saku Tabarmar ta karaso tana cire takalmin kafa ciki ta yar a nan ta haye tabarmar tana kallon abanta Sai kawai ta sheke da kuka harda tafa hannaye ta ce" Mahamadou Rasululahi sallalahu alaihi Wasallam Abana haka ake mutuwa? Ba accident ba, ba gobara ba abana gawa biyar biyar abana, wayo allahna abana kashi a fili, abana ashe aikin asibiti da kace ba zan iya ba inada saurin kuka na maka gardama haka ne?, Ai kam na yarda yanzun ba zan iya ba, gwarama a sakani wajen koyon dinki na koyo na ringa yiwa yan anguwa inda samun na sakawa a bakin salati" Aba dake ta amsa salatin da ta yi da kula sosai ya ce" Asha, asha asha, to in ba autar Aba ba rasuwa ai kulun yinta ake yi, kuma kin san mafi yawancinta daga babar asibitinku ake fitar da ita, kin san gari ya girma ba yau ba al'uma ta cika, kuma harda kauyuka, idan lokaci ya yi dole a amsa kiran mai sama , Allah dai ya sa mu cika da kyau da imani, ni abinda nake sha'awa a aikin asibiti har nake tsayuwar dare ina kai kukana wajen Allah ya nunan irin ranar nan tarin ladan da kuke samu, yau a kawo maka marar lafiya ka masa sannuma lada ne bale ku da zaku cencana ku bi ku wanke jinni ku gyara waje, Allah ya sa sanadiyar shigarki aljanna ne wannan hanya Khausar dina" Tsuru ta masa tana kallon yannayinsa Kasa kasa ta ce" Abana, wai da cewa na yi fa an fasa aikin , tunda na je ban ci komai ba fa ina ta aiki ina ta aiki kamar in summa, wai da cewa na yi mu yi shawararmu da kai sai ka cewa Mama ka soke aikin asibiti ba zan koma ba ko Abana?" Shima ya rage muryar sosai ya ce" kina nufin dan kawai kin dan wanke jinni kin ga gawa shikenan har kin karaya? Bayan kece mai kokarin a gidanma kaf? To da kike cewa fata kike ki fara aiki ki siya min babur in kika fasa da me zaki siya min kennan? Da kike cewa keke zaki koma shekara nawa zaki dauka kafin ki koya kuma ki dawo ku layu da su maman ummi wa za'a ba dinkin wa za'a hannawa? Ta yiwuma ke sai dai ki ringa dinkan jalabiya kawai a gidan, ni dai ina so ki yi aikinki abinda wahalar ta dan lokaci ce, na wata uku ne fa kawai, kamar gobe ne, kuma abincin da komai ni zan ringa kai maki fa, daga kasuwa zan je na kai maki sai in dawo, ni zan ringa rakakima fa" Wani irin fadawa da ta yi a tunani sai ka tausaya mata ka kuma yi mamakin du girmanta shekara kusan ta ashirin da takwas ama mahaifinta ya yi mata wayo a dan kankanin lokaci, koda yake dama Khausarar aba ba dai rashin wayo ba A sanyyaye ainun ta ce" Aba, ina jin tsoro, kuma akoy wahala sosai" Da kula, zuciyarsa cike da tausayinta da tarin tunanin inama zai iya hannawar, da ya hanna, sai dai ya san abu ne da ba zai yiwu ba, du irin shekarun da ta dauka tana karatun nan Allah ya fitar mata da hanya ai wahala jurewa za'a yi kawai, dan haka ya ringa karfafa matya gwuiwa da kula yana nuna mata cewar ai wahala bata kisa, kuma Wajen nan da aka kaita zata matukar jin dadi zuwa gaba domin zata koyi aiki ne hannunta ya kware sosai har sai ta zama abin alfahari ga kowa da kowa A cikin hirarsu ne yake mata maganar Yaya aka yi Mujaheed ya zo ya yi ta zama? Nan ta sanar masa basu yi zai zo ba, wayartama a gida ta bari, harma ta fada masa abinda Mujaheed din yace A gabanta dai Aba bai nuna komai ba karshema saka ya yi ta shige wanka tana fitowa ta gaisa sosai da mamansu sannan ta shuge dakinsu, kafin kace me wannan barci ya yi awon gaba da ita A lokacin da Aba ya shiga daki sosai ya nunawa Mama damuwarsa da damuwar yarsa, Mama ta bashi baki cewar idan aka jure yanzu abin zai wuce, dama aikin asibiti aiki ne mai girman gaske, dole za'a sha wahala idan ba'a saba ba, ama a hankali komai zai daidaita Numfashi ya fitar zuciyarsa na masa wani kaikayi,, abin ke sukarsa har kamar zai amayar ya sanarwa mahaifiyarsu ama kuma ya rike a ransa A maganar Khausar maganar Mujaheed ta matukar daga masa hankali Anya akoy zaren mutunci a yarensa kuwa Shi zai fitar da su daga gidan nan ya kaisu wani, da ta bashi dama da tana hawa motar kanta? Me kennan? Gaba daya sai zuciyarsa ke son gannin haka a matsayin cin fuska ko sharar fage dan ya kangarar da zuciyar yarinyarsa, idan har mai kwadayi ce maganarsa na iya sakata yiwa abin wata fahimta daban, shi bama maganar rabuwarta da TAUFEEK ya tsaye masa a rai ba, dan ya san dama idan har ta yi aure ba kowanu namiji bane zai iya hakurin mu'amalar nan, kuma summa ai yana gannin hakan ba zai iya zama matsala a tsakaninsu ba, abinda yake iya yiwa hasashen na iya zama matsala a lamarin nan wani taku da ya hango wanda da wahala ya iya jurewa, watau wulakanci Eh lalle shi talaka ne Kuma yana zaune a anguwar talakawa, yana cin cimar talakawa Ama hakan ba zai ba kowa damar wulakantashi ko wulakanta masa ya'ya ba Bai je ya roka a wajen kowa ba Bai je ya yiwa kowa maula ba dan ya san ba mutun ne zai bashi ba sai Allah Bai wulakantar da kansa ba ko a anguwa bale a kasuwa uwa uba a gaban sirikai Ba zai lamunci komai mai kama da cin mutunci ba Shi yasa ko maganar auren su Aisha da aka saka ranar amsar sadaki da kaya nan da kwanaki goma sha biyu bai zurma ya yarda aka ringa ba ya'yansa abinda ya shafi kudi ko abinda ya fi karfinsa ba, ko sun amsa a rashin sanninsa ne, baya yarda baya bada kofar nan, dan ya san babu wanda ya iya rikita zuciya irin dan Adam, saima ya nuna maka duniya kaine ya yi tsaye ya watsaka Ajiyar zuciya ya sauke bayan ya kai hakarkarinsa ya kwontar, a ransa ya gana yanke hukuncin sai dai Allah ya ba Mujaheed hakuri, domin ba zai dawo kan maganarsa ba gaskiya, ba zai gaba yarjewa Khausar amsar abin hannunsa ba, ba kuma zai masa maganar ba shiruma magana ce zai gani ne a aiyukansa cewa bashi da abinda zai basu ya ciresu a talaucin da yake gannin sunna ciki! ___________________________________ Du irin yadda ya so ta sasauta yannayin tsoron da take ciki nasa abin ya faskara Dan murmushi ya yi yana kallonta, ta yi jajajir kamar an konata da ruwan zafi, sai hadiyar zuciya take yi tana sisine kai dan kawai yace sai ta ci abinci ya dubata kafin ta kwonta, haka ta wuni a kwonce waje guda danma ya wuni wajenta ya mata dukkan taimakon da ya dace domin har karin ruwa ya jona mata ya san jikinta ba maganar ciwo a yanzu sai dai ko ta saka tsoro a ranta ne bayan shi ya san a haka din ya yi iya yinsa dan kiyaye sakata a halin tsoron, ta so ta fi karfin tunaninsa ne har ta saka shi aikata haka domin bai yi niya da wuri haka su saje ba, sai gashi abu ya faru tsakaninsu a lokacin da bai shirya din bA A hankali ya mike daga zaunen da yake ya mika mata hannu ya ce" Taso mana, wai ko ban duba da kyai bane kar aje kin karu, mu gani?" Gabanta ya sake faduwa, curewa ta sake yi waje guda a saman gadon tana rintse ido tana jin tsoron kar fatarsu ta sake haduwa ta ji azabar da ta ji a yau Bafa kokari ne bata yu ba, ta yi kokari fiye da tunanin bawa, abin ne ya girmami rashin hankalinta, ta yi dana sani da ta matse masa waje, ashe sanyin halinsa na macijin kumba ne sari ka noke? Ashe shi din wuta ne mai zafin gaske? Ashe hasashe ne take yi da akace da ya gama ta mike ta murje kamar ba'a yi ba? Gashi dai an yin an gama ama ta kasa mikewarma bale har ta murje kamar ba'a yi ba in ba dan an turo mata wace ta sake tayata kimtsa kanta ba da bata san yaya zata iya koda cin abinci bane Da rarashi da komai ya bata kula daidai gwargwadon iyawarsa har ta samu barci Murmushi ya yi yana dauke dubansa a kanta , tunani yake na lamarin rayuwa Shi dama ya san a yanzu da take bakuwar lamarin ya fi karfin halitarta, sai dai mace rijiya ce ya san du wahala zata jure kuma du irrin abinda zata nuna a sannu zata saba Shi likita ne baba ya san dalilin da ya sa ake so a bi mace a hankali har hankalintaa ya dauka Murmushi ya sake yi ya karrasa saman salaya, ya shiga gabatar da ibadaraa cikin nutsuwa, Sai kusan biyun dare ya kwonta, dan zai yi fitar wuri ne zuwa wajen aiki ga kuma kasuwa Aba ya fara maganar yana son sakar masa aiki shi kadai _________________________________ Tunda sasafe ta shirya, Yau Aba ne tsaye kanta da zazafe tana turawa yana karra fadin ta karra ko kadan ne, abin har tausayi yake ba Mama idan tana kallonsu, soyayar Khausar da mahaifinta daban take kuma a bayane take Tana gamawa ta sake yin bruch ta kuma shan panadol dan ciwon kan ya ragu ama bai daina ba gaba daya A cikin hijaban da suka sha mamakin yawansu ya dauki daya ta saka a jakar da Aisha ta bata Sosai Mama da yan uwanta ke karfafa mata gwuiwa sukai masu rakiya har bakin kofa A kafa suka taka da Aba, sunna tafe Aba na ta yakin cire mata du wani kyankyami ko tsoro a ranta, yana nuna mata romon abin da sauransu har suka isa bakin likitar sannan ya bata dari biyar dinta cewar ta cin abinci ce Haka dai ta rabu da Aba kamar an kawo yaro karami makaranta ranar farko tana ji tamkar ta bi shi da gudu ta su komawarsu gida Haka ta saje ta ringa aiki tamkar ba gobe har kusan sha biyu mai gadi ya miko mata abinci cewar inji Abanta a nan ta kula ba abinci bane basa ci cin ne a tsaitsaye ba a nutse ba saboda aiki,kuma gannin jinni ko wani abin baya hanna su ci , sukan ci ne su ci gaba da aiki A ranarma sai dare aka salameta ta nufi gida ta kuma tarda wani rikicin sabo na Mujaheed domin sai ya nuna ta ajiye wannan aiki zai sama mata clinik tunda bata da lokacinsa, karshema ya nuna shi faa gidansa bama zai iya barinta aiki ba, ita daita bashi hakuri sosai ta lalabashi suka rabu lafiya A hankali kwanaki ke ja, har lokacin taron amsar sadakin Kannenta ya zo,ranar da ta yi iya yinta dan hanna kanta kuka, ba dan komai ba sai dan magangannu da ta ringa tsinta kala kala masu firgita zuciya da rikita tunanin bawa da saka bawa saka kansa a mugun tunani marar anfani Kasancewar yan matan anguwa da na makaranta sun taru , ga tsofafin anguwa da datawa, kowa albarkacin bakinsa yake fada har zaman ya nemi gagararta a cikin mutane sai samun hanya ta yi ta fice a gidan ta nufi asibiti bisa umarnin Mama da itama tata zuciyar ta cinkushe gannin yannayin na khausar, bayan idan an tambaya ana fadawa mutane cewa tanada manemi magana ne bai yi ba a gaba, ama sai an bita da magangannu gasunan dai mararsa dadi Tana zuwa ta samu doctoe Rauda ta kama mata aiki, a yanzu an fara bata dama irin ta saka allura da cirewa, wanke kurji da sauransu, haka kuma ta fara samun dama irin ta sakewa a cikinsu Da wuri ta fito yau dan kiran da TAUFEEK ya mata cewar sunna gidan A lokacin da ta karaso ta tardo ya zo daukan Hajia ne tare da matarsa, nan suka gaisa da Yumnah sama sama dai , ama ita sam bata gane ba dan hankalinta ba a nan yake ba a tunani yake wanda ke neman hanna mata sukuni Sunna fitowa suka shiga mota TAUFEEK ya dawo ya dan zuba mata ido, du ta zube , kana ganninta kaa san ba jikinta bane , gashi yau harta lebenta a bushe yake kamas tsabar tunani da takura rai A sanyaye ya ce" *ALLAH BAI SAUKAR DA CIWO BA SAI DA YA SAUKAR DA MAGANINSA* Ni ce dai Fareeda Abdallah, na sake dawo muku da tallen magungunanmu da zuwa yanzu bazan iya ƙayyade yawan waɗanda suka dace da biyan buƙata sanadiyyar amfani da maganinmu ba. Alhamdulillah! Ƴar'uwa ki gwada, wataƙila warakarki na tattare da maganinmu. Haihuwa ce baki taɓa yi ba ko kuwa jinkiri kike samu sanadiyyar planning ko kuma haka kawai? Muna da ingantaccen maganin rashin haihuwa ga mace da namiji, wanda za ki bada sadakar 2k ga matsalar ko wane ɓangare. In sha Allah za ki dawo da godiyarki bayan amfani da maganinmu. Sanyi (infection) ne yayi miki yawa yake saka ki ciwon mara, zubar farin ruwa, ƙaiƙayi, ƙuraje, ɗauke ni'ima, har ma ya saka mijinki ya dinga miki gani-gani saboda bakya gamsar da shi? Da naira 3k zamu haɗa miki magungunan da za kisha ke da Oga in dai kika yi amfani da su ku da sanyi har abada in Allah ya yarda. Muna sayar da ingantaccen haɗin sabaya, wanda zai sa nonuwanki su cicciko, hatta fatar jikinki sai ta murje sanadiyyar shan kunun sabayarmu. 2500 bokiti 1litter. Muna da maganin wankin nono ga mai ciki da mai shayarwa, wanda indai kikai amfani da shi yaronki zaiyi tubarakallah, ba ruwanki da laulayi. Muna da ingantaccen maganin Daji (Cancer), typhoid, maleria, yaron da yayi nauyin ƙafa, da sauran cututtukan da ban ambata ba. Muna aika maganinmu ko ina tsakanin Nijar da Nigeria, ga masu buƙatar magani da gaske su tuntuɓeni akan lambar wayata 07039080978, ko 09077591726 Noted: *MAI SON MAGANINMU IDAN BA A KADUNA YAKE BA, SHI ZAI YI KUDIN MOTARSA HAR ZUWA INDA YAKE, BABU INDA BAMA TURAWA IN SHA ALLAH.....SAI KUN ZO* 💔💔💔💔❤‍🩹❤‍🩹💔💔💔💔 *DA CIWO A ZUCIYATA* 💔💔💔💔❤‍🩹❤‍🩹💔💔💔💔 _MALLAKIN_ *SAJIDA NIJAR* *FREE BOOK NE* 2️⃣1️⃣ LITATAFAN MARUBUCIYAR Duk karyar kada Yar mahaukaciya Neman na kaina Bani da zabi Bak'a ce Kutkale Makauniya ce Mage Duk nisan jifa Idan ka raina inda kake Dutse Alkalamin kadarata Bani da zabi Dakika Biyar Now *Da CIWO A ZUCIYATA* *Tallah, tallah, tallah* *SECRET DE LA FEMME DU MANGA* _Gidan Kamshi, Sirrin Manyan Mata, nesa tazo kusa,Amarya ,Uwar gida,Ango da mai gida Har ma da yan mata da samari shin kuna sane da cewa HAJIYA FUSAM ta shirya tsaf domin gwangwaje ku da turarakunta masu dankaran kamshi? Tare Kayan gyaram jiki na musamman ,wanda daga nesa kamshin ki kadai ya wadatar ya isar da sakon zuwanki waje,gidan ki kuwa sai ya zam abun kwatance wajen kamshi, kar na cika ku da surutu bara in fara zayyano su_ Farar Humura Bakar Humura Humura special, humura de bain Humura epicé Lait de nuit Parfums désodorisant Parfums rideau et dras Lait de nuit Alkam Kulakcam *Waɗannan kadan ne daga bangaren turaran ruwa* Gagab, sandal flex, Durot, durus, sandal fleur, tafarce, farce, sandal bangui, sandal, hypotonic sandal, al'ut, coktail creation VIP, Gajiji, Mankaji, turaran wutar labule da cafet, Aba malan, boulettes *Munada bangaren gyaran jiki kamar haka:* mai mai saka santsin jiki, mai mai kanshi, Kayan gyaran jiki mai saka fata ta yi santsi da laushi, kayan gyaran jiki mai saka fata ta yi fari, Sabulu mai saka fata ta yi haske, sabulu mai saka fata ta yi santsi, sabulu mai goge yanayin fata, mai wanda baya saka fari mai gyara fata Sayen na gari mai da kudi gida,sai an gwada akan san na kwarai💃💃 Hajiya Fusam na zaune a kasar Niger domin yin magana da ita kai tsaye tuntuɓi wannan number 97 82 44 94 *SECRET DE LA FEMME DU MANGA* Gidan Kamshi, Sirrin Manyan Mata💃💃💃💃💃 A sanyaye ya ce" Yauma kin yi aiki ne?" Fuskarta ta dago a hankali ta zubawa tasa ido, kwanakin nan da ta yi kusam biyar bata ganshi ba saboda aiki ya yi tsanani sai ta ga ya wani cika kasumba a fuska, ko idannuwanta ne ke nuna mata haka? A hankali ta sauke ajiyar zuciya ta dan girgiza kai tana kawar da dubanta a kansa ta kai wajen motar Ido cikin ido suka yi da Yumnah Da kallo wani kalla wanda idannuwanta suka gane mata daga idannuwan Yumnar, wani kallo daban kamar , kamar dai, kamar........ "Uffff, ya salam" ta fada a hankali tanaa dauke nata idannuwan, domin abu daya ranta ya bata shine yannayinta na son taba mata kwakwaluwa bayan zuciya "Kina da wata damuwa ne?" Ya sake fada, domin gaba daya yannayinta ke neman taba nasa yannayin A hankali ta girgiza kai tana kokarin daidaita yannayinta ta ce" Ba komai" Zuba mata ido ya yi, yana gannin kwalar da ta maida karfi da yaji, naan fa ya ji hankalinsa na neman tashi Ya san wacece wannan yarinya ciki da bai Kasantuwarta mai tsananin rauni , mai mutunci mai mutunta kowa, mai farin cikin badawa, mai zama da zuciya daya ya saka ya shaku da ita shakurwa irin ta mamakin nan, domin yakan rikice lokuta da dama da damuwarta "Yaushe kika fara boye min damuwarki?" Ya fada a hankali yana so lalle sai ta kalle shi Dagowa ta yi lokaci daya idannuwanta suka ciko da kwallah mai zafin gaske ta saka idannuwanta cikin nasa A hankali hawayenta ya shiga wanke fuskarta har ya zamto ta dan fara shasheka tana kallonsa cikin hijab dinta milk color wanda ke boye sirrin jikinta gaba daya Ido cikin idon nan bataa dauke nata ba dan tana nitsewa ne a cikin idannuwansa idan har tana hali na kaka nakka yi, takan samu solution ne a nasa idannuwan dan takan ga tausayi, karfafa gwuiwa, fada, jajircewar sai ta yi hakuri a nasa idannuwan a kan dole A hankali taa shiga fadin" shin menene nakasata? Har yau ka ki kaa fada min, ko da ake cewa nauyin jikina haka din ne? Shin na yi mugun nauyin da za'a riga raina min wayo ne ? Anya Mujaheed zai aureni kuwa? Yau da gobensa ya fara bani tsoro, bayan dukkan biyayar da ya dace ace na masa ina kamantawa hharda wace bai dace ba domin tun kafin na shigaa gidansa ya dora min dokoki irin masu tsaurin da idan ka ji kana iya yin fushi da ni,ama shiru kake ji bayan a da shine da kansa yace ana yin sallah zai turo, gashi yanzu an fara irgen kwanakin babar sallah,....." Ta langwabe kai ta ci gaba da fadin" idan na yarda iyyayena suka ga hawayena a yau tanar farin ciki yaya zamu kwashe ne? Idan kuma suka ganni gani gododo Rukaya kanwata ta baya an saka mata rana yyaya zasu iya rintsawa ne? Gashi ranna ce baba, rana ce da gidanmu kaf ya dace ace muna cen muna shagali, shin na fara yiwa ahalina baakin cikin samun farin ciki komenene nake ji a nan ya tsaye min a daidau kahin zuciya? TAUFEEK inada ciwo mai girma a zuciyata wanda nake rainonsa tunda na kai shekaru goma sha bakwai a duniya, domin nan da ka ganni tun inada sha uku Mama ke dan tare tana fadin zata ga autanci idan na kai sha bakwai Aba ya mikani dakin miji, a yau shekarata ashirin da bakwai zuwa da takwas, tun tana jefa yan kofunna da kwanoni Aba na hannawa a taba cewar nawa ne har wasu suka lalace aka zubar wasun kuwa a dole aka fitar muka yi anfani da su a cikin gida, TAUFEEK yannayin jikina zai iya hannawa na auru ne ni na hakura gaba daya ko menene? Ko dai bani da lafiyane? Domin wasu na cewa ko ina fama da bakin aljani ne?????" "Ke uban wanene ya dake ki iyi?" Muryar Hajia ta katse mata hawayen da take yi da kuma maganar da take masa mai kamada rada wace take fitarwa daga zuciyarta tana sanarwa mutun daya tak da take iya sanarwa a duniya *KAF DUNIYA BATA DA SIRRI SAMA DA TAUFEEK* , kaf duniya bata da da sirrin da take gannin bai sani ba, komai ya sani nata, kamar wani wanda sukaa girma tarr bayan ya bata tazarar shekaru , asalima bai fi shekara hudu da suka san junna ba Da kyar ya iya sauke dubansa a kan Hajia, wace ta kamo kumatun Khausar tana gyatsine ta ce" Ke dilla kalle ni nan, nace uban wanene ya dake ki? Ke yanzu a haka zaki zauna ki yiwa wani kuka? To na cire maki mutun biyu, ita ko shi wa'inda suka kawo ki duniyar, bayansu du wanda ya san ya dake ki fada min sai inda karfina ya kare, aikin banza aikin wofi ni du sai na ga kamar kin rage kumari daga gannin karshe da na maki, kumatun nan naki kamar sun rage auki, dan mu ga dagen hijabin mu gani....." Da sauri ya rike hannun Hajiar, har idannuwansa na yin waje, jasa kasa ya ce" Cire mata hijab zaki yi a waje ?" "Igiyar uban wani ke kanta da zan ki gannin kumarinta a waje?" Ta bashi amsa tana maka masa harara sannan ta kama hannun KHausar ta ce" Ke maka maka share hawayen maka, wuce mu je" Da ido ya iya binsu, jiki a sanyaye ya juya ya nufi motar ya bude ya shiga sannan ya saka hannunsa a hankali ya dafe wajen gemunsa yana hangen kofar gidan inda Hajia ke magana da Aba wanda zuwansa kennan ya dan zagaya dan amso ruwan piyawata don su yi anfani da shi a gidan Hajia kuwa abinda ta fadawa Aba ya saka shi yin murmushi yana bada hanya ya ce" Kai Hajia ni kam ai bani da ta cewa Khausar ai taki ce" Ta sake sakin wani murmushi ta ce" Mamuda ko, kai dai an yi dan mutunci walahi bara na karbo completinta ko ashirin ne mu je, yar nan sai na tashi tsaye a kanta inaga sam ba'a san ciwonta ba" Shi dai hanya ya bata ta shige, kafin ya sauke ajiyar zuciya, godiyarsa ga Allah da take da wajaje na jin sanyi a zuciya, ya sani zata dan sake tare da hajia kuma har cikin ransa ya yarda da Hajiar bashi da damuwa da tafiyar Khausar din gidanta na kwana biyu Sunna shiga Hajia ta kirayi Mama gefe ta rage murya sosai ta ce" Kayan yar nan zaki bani mu je tare, wai kin kula kamar ta rage kumari kuwa? Yadda na ci burin auren yar nan harta gado nice nan zan mata bana son na ga tana rage kumari, wai kina bata yan jiko da su yusufa dan karro farin jinni kuwa? Sai fa da yan jiko da turare turare saboda makiya, yau ko dan yannayinta sai fa ta tsole ido, dan dauko min ko kala ashirin ne mu je kin gane?" Mama ta amsa da to,sannan ya yi dakinsu da dan sauri Jim kadan ta fito dauke da yar akwati dauke da kayan na Khausar, dan a shigarta sai da ta tabo Aba , yaba dagawa ya sanar mata su tafi dan haka ta sauke ajiyar zuciya ita dinma ta hado mata harda yan baby hijab dinta da hijabinta baba da kalolin kaya uku Hajia ta amsa tana washe baki ta yi gaba ta bar Khausar tsaye wace ido ya cikowa da kwallah takasa bin hajiar ta kuma kasa cewa komai A sanyaye tana kallon mamanta ta ce" Mama" Mama ta sakar mata murmushi a hankali ta dan shafa gefen fuskarta ta ce" Ki je Khausar din Aba kin ji? hajia ce ai , kin ga tana sonki ki yi kokari ki kiyaye abinda zaki batawa kowa rai kin ji? Idan kina so gobena sai ki dawo ko?" Khausar ta gyada kai a hankali sannan ta juya, tana ji wani irri, dan tunda take bata taba kwana ba a gidansu ba, komai nisan waje tana dawowa ne ta kwana a gida Da ta fito bata ga Aba ba, a dole ta karasa wajen motar ta bude baya ta shiga dan Hajiar da TAUFEEK ne a gaba, Yumnah kuwa a baya Dan murmushi ta so sakarwa Yumnah, sai ta ga gaba daya ba bangarenta take kallo ba A hankali ya dan saita madubin motar ya kalli fuskarta, ba dan komai ba sai dan ya ga shin zata iya zuwa gidansu ta kwana da son ranta ko karfa karfa hajia ke son yi mata Yannayinta bai kare shi da komai ba sai karin wani tunanin da damuwa, dan kasa take kallo da dara daran idannuwan nan nata sai busasun hawaye da suka kwonta a saman kumatunta A nutse ya tuka su har suka karasa gidan Sunna zuwa Hajia ta bude , sannan ta bude bayan ta janyo hannun KHausar tana fadin" Mu je , yi maza ba fara saka ki a ruwan kaka ka yi ka fito, sai an samo maki ki bugo wannan hawaye haka, ina ba zai yiwu ba!" Da ido suka bi su har Hajiar ta shige bangaren su Maman TAUFEEK, wa ya san me zata yi a cen din Motar ya rufe ya zagaya inda hajia ta bara masa jakar shi dan aikenta ya ciro jakar sannan ya rufe da nufin mika masu jakar Da sauri Yumnah ta riko hannunsa, hakan ya sa ya juyo yana kallonta da dan mamaki, domin a sanninsa rabonta da ta kai hannunta da kanta jikinsa tun wayewar garin nan kafin komai ya shiga tsakaninsu Fuskarta a marairaice sosai ta ce" Ama, ina zaka je ne?" Dan tsai ya yi yana kallonta, ya san a yanzun kamar ba wata jituwa tsakaninta da Khausar, dan haka a hankali ya ce" Jakar zan ajiye masu" Jakar ta kalla, da sauri ta miko hannayenta ta ce" Aa gani kuma zaka kai, kawo na je na kai masu ka shige ciki na dawo na zuba mana abinci ka ji yayanmu?" Bai kawo komai ransa ba ya bara mata jakar, duda ya so ya dan zanta da Khausar sai dai ya san abu ne da kamar wuya dan a yadda hajia ta yi raf da ita din cen da wahala ta saketa Ciki ya shige, ita kuma ta ja tsaki ta riko jakar kamar ta rike kashi ta kai cen bangaren hajiar ta yar da jakar a kofar falon Hajia sannan ta juya ta yi tafiyarta, dan ita tunda ta zo gidan nan kafarta bata taba shiga bama cikin falon Hajia saboda karara ta gane ba wani sonta take yi ba, ba zata ringa kai kanta inda ba'a sonta ba gaskiya, haka ta koma ranta cike da jin zafin hajiar na wannan sabuwar fitinar, a kan wani dalili zata dauko katuwar mace tana wani kama kumatunta tana share mata hawaye tana masifar da bata san dalili ba ta kawo mata gida inda mijinta ke nan? Bi izinillah daidai take da uban kowa a kan TAUFEEK, ta gama yarda cewa ya isa ta yi kuma idan ta yin ba laifi ta yi ba shi yasa ta sake daukar damarar bashi dukkan kulawar da ta dace, ciki kuwa harda mayar da shi baban waje du kuwa da tsoron da take , zata bashi hadin kai dari bisa dari ta yadda zai manta da wata jibgaga abin haushi gidan tsami kawai! A bangaren Khausar kuwa ta ga abin mamaki gannin idonta Wanka dai mai sunnan wanka sai da Hajia ta sakata ta yi sau uku na magunguna Maman TAUFEEK na tsaye tana rike da kwaryar, Hajiar kuwa tana hadawa tana bata tana fadin idan fa bata yi ba shiga zaki yi ki darzar min ita dan na kula shashanci na damun yar nan banza sai sakin hawaye take ta ki fada min ubanda ya daketa, danma na san shi Magidanci ba zai daketa ba ai da tuni na samu mai kwanoni a waya ya min tsakani da shi, har ga Allah yar nan ta gama sacen zuciyata sai yadda hali ya yi kuma, ji nake uwa in janyo nesa ta zo kusa in samo mata gagarumi rikaken dan arziki ya kwasheta mu tafi" Ita dai Mama tana tsaye har ta gama ta fito da katon hijabi nan kuma aka kuma saka mata kaskon hayaki Khausar kifta ido kawai take tana kallon Mama dake murmushin hajia tana fadan Magidanci yau bai zo ya yi hayaki ba yana cen shi mai mata abu kamar a karye ana fama da katon hanci da feleke da waya ƙatuwa Kai magidanci ya dauko da zafi mace ba mamora da ramin kashi Ana gama mata turaren Hajia ta wuce cikin kicin wai zata zubo mata abinci, nan Mama ta zauna bayan ta ciro mata kaya cikin kayanta tana kallonsu da kula ta ce" Daughter me yake damunki ne? Hajia sai fadi take kina kuka?" Khausar ta sada kanta a hankali ta girgiza kanta ta ce" Mama, ba komai fa, kawai dai abin bama wani bane Hajia dai ta yi tunanin ko wani ne ya sakani kukan" Mama ta yi murmushi tana sake kallon Atampar, sam atampar bata wani yi mata ba, ama kumaa bata nuna ba ta bar abinta a ranta da kudurin dake ranta ta ce" Ai kam kema kin ji jiki tunda Hajiata ke kaunarki, ke da Magidancin zaku ji jiki iya jin jiki" Dariya Khausar ta yi itama kadan tana amsar atamparta ta mike ta shige ciki ta saka tana ta jan rigar gannin tana neman fado mata , gaba daya rigar ta mata yawa yanzun bayan a da har da kyar take numfashi a cikinta, zanin dai ne daidai ta daura ta sake zumbulo hijabinta ta fito Tana shirin zama Hajia ta watsa mata harara taa ce" Ke dilla cire hijabin, haka fa take yawo yadda kika san yar aike da hijabin nan,, ba dole a yi shiru ba wannan zamani da ya zama na dan kyale kyali, ni hijabinma haushi yake bani in ba dan kar a min wata fasara ba sai nace ina dalili ne wai? Cire ko sai na tashi?" Mama ta zarro ido tana kallon Hajia da kokarinta, Khausar kuwa ta cire din ama kuma ta kasa ajiyewa bale ta zauna, bama kamar yadda kitsonta ya tsufa kuma kan ba hula, ga yadda rigar ta mata sai a hankali Da ido Hajia ke nunawa Mama bayan Khausar, Mama kuwa ta ki kallo kawai ta cije abinta dan Allah kadai ya san dariyar dake cinye mata zuciya na lamarin Hajia, haka kawai ki dauko yar a gaban iyayenta kice basa sonta ke zaki kulata? Ga yarinya mai kunya sai sinne kai take ama Hajia ta ki fahimta, karshe dai haka ta sa Khausar cin abincin nan sosai sannan ta sakkata shiga daki ta kwonta suka ci gaba da tataunawa da Mama kafin ta mike ta koma itama Tana shiga falonsu ta samu abokiyar zamanta zaune tana fira a waya Da hannu ta gaisheta ta shige ciki dan ta ga tana waya, ita kuwa ta rakata da matsiyacin kall9, duda tsohon cikin dake jikinta bata rasa fitintinnu a tare da ita, a rayuwa taren Hajia mahaifiyar mijinsu da matar mijin nasu uwar TAUFEEK na matukar ci masu tuwo a kwarya, hajiar nan basu taba gannin fitinaniya irinta ba, gashi idan bata yinka bata yinka ne babu wanda zai sakata ta yika dan dole ko waye shi, shi yasa lokuta da dama su da ita a je a gaisheta ne a tashi dan idan ka zauna yanzu wani abin zai faru ta balo maka ruwa, sun yi sun yi su lalata taren nan abin ya faskara, ko yanzu da ta zo ta jata suka wuce ya sa dayar mikewa ta shige dan haushi, ita ta zauna dan so take ta ga abinda aka yi ___________________________________ "Idan baki saka pankeken nan ba babu inda zaki je Khausara, kin ji dan uwan rahamanu babu inda zaki je, yau ga aikin banza aikin wofi, hakaa kike son fita ki je wajen aikin? Ai ba kabari za'a saka ki ba, kina abu kamar wata ni? Ko ni kajal nake radawa in fuske bale ke yarinya danya shirat budurci a leda!" Ta ajiye maganar tana sake gogo mata hodar da ta je wajen yan matan gidan ta amso da kwali da jan baki wai aro kafin a jima ta je kasuwa ta siyowa Khausara pankeke A tsaye yake a kofar dakin, cikin shiga ta kayan aiki , ama babu abinda zai iya ce maka ga aikin Kanshi yake fitarwa ta ko'ina, hannunsa dauke da agogon dake nuna masa takwas ta kusa , gashi a tsaye ya kasa shuga saboda Bakin hajia da kalaman da take fada tun dazun sai yake ganninsu da jinsu wani iri Turare ne Hajia ta rike kuuuuuuu tana fesa mata , sai kuna ta dauko wanda ta zo da shi nata ne da ta siya wajen HAJIA FUSAM mai turaren yan gayu ta bude shima ta yi mata feshin albarka dan sai da dakin ya dauki kanshin gaba daya sannan ta rufe tana fadin" Yauwa ko ke fa, ga farar rigar ga kuma dan karamin hijabin, ki je ki dawo mi je wajen tela Allah ya tsare bara na ba direba abincinki" Daga daga nan Hajiar ta wuce da kwondon da ta zuba mata abinci lafiyaye ta bi ta kicin Ajiyar zuciya ya sauke ya girgiza kai sannan ya daga labulen da niyar ce nata ta zo su gudu kafin hajia ta dawo ta hadasa masa ciwon barin kai Hankali ya zuba mata ido, Atampa ce a jikinta mai haske, dinkin doguwar riga ne wanda ya dan mata yawa daga wajen tumbi dan zazagewar da tumbin ke yi ama kuma ya rike cinyoyinta tak dan kamar nan jikin ya karra komawa, sai dan madaidaicin hijab din da Hajiar tace shi zata saka ta yi tsuru tana tunanin halin da take iya shiga idan ta fita a haka domin ta san babu inda zata iya zuwa Da ido yake kallon fuskarta gannin ikon Allah su jan baki, su kwali su pankeke in ji hajia, daidai itama ta dubo gannin an dage, dan haka ta ja numfashi da sauri ta karaso inda yake tsayen, hakan ya saka dadade, nutsatse, hautsinanen, fitinanen kanshin turaren fara isowa kafin ita, a dan rikice ta ce" Dan Allah dauko min hijabin baba freind idan na fita sai na saka, ni kam na bani da rikicin hajia wai a haka zan fita fa" Idannuwansa ya dauke a kanta ya sauke kan uwar daban, ita dai matar nan baba a wajen mai kwanoni, da ta dawo fuska na mata gyatsine kamar tsantsamen kunnun safe, ta wani cakare irin ko wace wace tana sake kankance ido ko ganne shi ne bata yi ko me take nufi oho? Fuska ya daure sosai yana kallonta ya ce" Wannan tsohuwa bata son zaman lafiya🙄🙄🙄 *ALLAH BAI SAUKAR DA CIWO BA SAI DA YA SAUKAR DA MAGANINSA* Ni ce dai Fareeda Abdallah, na sake dawo muku da tallen magungunanmu da zuwa yanzu bazan iya ƙayyade yawan waɗanda suka dace da biyan buƙata sanadiyyar amfani da maganinmu ba. Alhamdulillah! Ƴar'uwa ki gwada, wataƙila warakarki na tattare da maganinmu. Haihuwa ce baki taɓa yi ba ko kuwa jinkiri kike samu sanadiyyar planning ko kuma haka kawai? Muna da ingantaccen maganin rashin haihuwa ga mace da namiji, wanda za ki bada sadakar 2k ga matsalar ko wane ɓangare. In sha Allah za ki dawo da godiyarki bayan amfani da maganinmu. Sanyi (infection) ne yayi miki yawa yake saka ki ciwon mara, zubar farin ruwa, ƙaiƙayi, ƙuraje, ɗauke ni'ima, har ma ya saka mijinki ya dinga miki gani-gani saboda bakya gamsar da shi? Da naira 3k zamu haɗa miki magungunan da za kisha ke da Oga in dai kika yi amfani da su ku da sanyi har abada in Allah ya yarda. Muna sayar da ingantaccen haɗin sabaya, wanda zai sa nonuwanki su cicciko, hatta fatar jikinki sai ta murje sanadiyyar shan kunun sabayarmu. 2500 bokiti 1litter. Muna da maganin wankin nono ga mai ciki da mai shayarwa, wanda indai kikai amfani da shi yaronki zaiyi tubarakallah, ba ruwanki da laulayi. Muna da ingantaccen maganin Daji (Cancer), typhoid, maleria, yaron da yayi nauyin ƙafa, da sauran cututtukan da ban ambata ba. Muna aika maganinmu ko ina tsakanin Nijar da Nigeria, ga masu buƙatar magani da gaske su tuntuɓeni akan lambar wayata 07039080978, ko 09077591726 Noted: *MAI SON MAGANINMU IDAN BA A KADUNA YAKE BA, SHI ZAI YI KUDIN MOTARSA HAR ZUWA INDA YAKE, BABU INDA BAMA TURAWA IN SHA ALLAH.....SAI KUN ZO* 💔💔💔💔❤‍🩹❤‍🩹💔💔💔💔 *DA CIWO A ZUCIYATA* 💔💔💔💔❤‍🩹❤‍🩹💔💔💔💔 _MALLAKIN_ *SAJIDA NIJAR* *FREE BOOK NE* 2️⃣2️⃣ LITATAFAN MARUBUCIYAR Duk karyar kada Yar mahaukaciya Neman na kaina Bani da zabi Bak'a ce Kutkale Makauniya ce Mage Duk nisan jifa Idan ka raina inda kake Dutse Alkalamin kadarata Bani da zabi Dakika Biyar Now *Da CIWO A ZUCIYATA* *Tallah, tallah, tallah* *SECRET DE LA FEMME DU MANGA* _Gidan Kamshi, Sirrin Manyan Mata, nesa tazo kusa,Amarya ,Uwar gida,Ango da mai gida Har ma da yan mata da samari shin kuna sane da cewa HAJIYA FUSAM ta shirya tsaf domin gwangwaje ku da turarakunta masu dankaran kamshi? Tare Kayan gyaram jiki na musamman ,wanda daga nesa kamshin ki kadai ya wadatar ya isar da sakon zuwanki waje,gidan ki kuwa sai ya zam abun kwatance wajen kamshi, kar na cika ku da surutu bara in fara zayyano su_ Farar Humura Bakar Humura Humura special, humura de bain Humura epicé Lait de nuit Parfums désodorisant Parfums rideau et dras Lait de nuit Alkam Kulakcam *Waɗannan kadan ne daga bangaren turaran ruwa* Gagab, sandal flex, Durot, durus, sandal fleur, tafarce, farce, sandal bangui, sandal, hypotonic sandal, al'ut, coktail creation VIP, Gajiji, Mankaji, turaran wutar labule da cafet, Aba malan, boulettes *Munada bangaren gyaran jiki kamar haka:* mai mai saka santsin jiki, mai mai kanshi, Kayan gyaran jiki mai saka fata ta yi santsi da laushi, kayan gyaran jiki mai saka fata ta yi fari, Sabulu mai saka fata ta yi haske, sabulu mai saka fata ta yi santsi, sabulu mai goge yanayin fata, mai wanda baya saka fari mai gyara fata Sayen na gari mai da kudi gida,sai an gwada akan san na kwarai💃💃 Hajiya Fusam na zaune a kasar Niger domin yin magana da ita kai tsaye tuntuɓi wannan number 97 82 44 94 *SECRET DE LA FEMME DU MANGA* Gidan Kamshi, Sirrin Manyan Mata💃💃💃💃💃 Fuska a hade ya ce" Ke, je dauko hijab baba maza ki sameni a mota !" Daga haka ya juya ya yi gaba ko gaisar da Hajiar bai yi ba Khausar ta yi tsuru tsuru ta kalli Hajia ta kalli hanyar da ya bi ya fita ta gaza koda daga kafarta ne bale ta dauko din, haka kuma ta gaza bin bayansa Hajia kuwa ta ja ta harde hannayenta ta ce" Yau sai na ga ni uwar mai kwanoni zaki ji magana ko wancen marar jin tsoron Allahn!" Khausr ta hadiye yawu da kyar A hankali ta ce" Hajia na tafi sai na sauko" Hajia ta washe baki tana gyada kai ta ce" Ni na san nice zaki fi kauna yar nan, a dawo lafiya ina nan ina jiranki" Tamkar an zare mata laka ta samu ta fito tana ta rungume hannu a kirji ta nufi motar dake parker dan alamun tsayuwar motar suka nuna mata yana ciki Da sauri ta samu ta fada motar ta rufo tana sauke ajiyar zuciya Juyowar da zata yi sai da gabanta ya fadi sakamakon kaifin da idannuwansa sukai mata a fuska yana binta da kallon me nace maki? Fuska ta marairaice ta ce" Yaya kake so na yi ne? Hajia fa na tsaye ka san ai ba zai taba yiwuwa na take maganarta ba ko?" Motar ya kunna , cike da jin haushi ya ce" Hakane, sai nine ai maraininki, nace nine tawa maganar ba a bakin komai ba, tunda na kula baki dauki damuwata a komai ba, jiyan nan kin rainan hankali abinda na hannaki kin sake yi, kuma yau kin kuma yi, sai ki ci gaba, ki ci gaba Khausar!" Daga haka ya ci gaba da tukin Sunna shigowa harabar asibitin ya lalubo face masque ya saka a fuskarsa cikin dabara sannan ya parker dan nesa ƙadan yana jiran ta gama saka farar rigar da baby hijab din, domin ba abinda ya dameta a nan ta cire dayan hijab din ta ajiye ta saka karamin fari kal mai kyan gaske ta kuma saka farar rigar Da yannayin tsokana ta dube shi ta ce" Ka kuwa san yanzu tsaf bake iya maka allura na maka karin ruwa da komai da komai?" Ido ya zuba mata, yadda take saki murmushi irin an fa fara kwarewar nan ya saka shi yin murmushin shima aman bai ce mata komai ba Ta dora da fadin" Na tabata idan ka samu kaima shekarar badi in sha Allah nice nan zan koya maka, dan bani kwondona na tafi " Kwondon ya juya baya ya dauko ya bata, sannan ya dakattar da ita ya dan daga farin kyalen da aka rufe kwondon ya saka kudi a ciki a hankali ya ce" A dawo lafiya likita" Kudin ta kalla tana zarro ido ta ce" Wannan fa?" Shima ya zarro mata idon ya ce" Kudin kifi da dambu ne " Idon a zarre ta ce" kuma duka wannan? Wannan ai sai na ciyar da likitocin emrgncy da shi " Ya yi murmushi ya ce" Ki tafi mana ana jirana fa" Murmushin ta yi itama tana kudurta zata dawo masa da kudinsa in ta sauka, dan babu abinda zata siya ga abincin nan Hajia ta zubo mata zai isheta ne, sai kawai t dan ja baya tana masa alamun sai an jima sannan ta juya ta nufi ciki A wannan ranarma sun sha aiki, aikin da a yanzu take iya cewa idan bata fita ba sai ta ji wani bari na zuciyarta na cen, du irin abinda idannuwanta ke iya ganni na tashin hankali abin ya zame mata wani jigo na barin zuciyarta domin a ranta take gama yarda cewar fitarta aiki taimako ne wa al'uma da ita kanta, idan tana taimakon marar lafiya a yanzu tana jin wata irin nutsuwa a cen kasan zuciyarta, in ta ga an samu an fitar da mutun lafiya daga emrgncy sai ta ji wata salama tamkar mutumen nan danginta ne Yau da wuri aka salameta, hakan har ya bata mamaki, domin tun bayan sallar la'asar aka ce ta shirya ta tafi gida, dama fitowar tasu suka sani basu san komawarsu ba, domin emrgncy ko manyan ma'aikata kan fita su je wani sa'in saukarsu ta zamto ba yadda suka sn zasu sauka ba, dan idan wani aikin ya samu dole su zauna, domin wani lokacin hargitsewa gidan ke yi sosai sai gyaran Allah Da murmushi ta fito saboda tsokanarta da abokin aikinta ya yi cewar yau za'a je a sha barci an tashi da wuri su Hajia Khausar Bata taba tunanin iya gannin TAUFEEK a wajen masu parking din motoci ba, sai ganninsa ta yi, hakan ya bata mamaki ainun, harma ta kasa boyewa ta ce" Aa, yaya aka yi ka san lokacin tashina bayan ba lokaci ne a kayade ba?" Dan murmushi ya yi yana basarwa ya bi kwondonta da kallo, ya ce" Baki ci komai ba hala tun safe?" Murmushi ta yi bayan ta shiga motar tana jan abu ta rufe ta ce" Na zatama zan iya ci tunda na zo da shi, sai kawai na manta da shi kwata kwata, sai yanzu da na shiga cenza kayana na ganshi kuma ka ga har ya fara bacewa ba damar na kyautar tunda nima ba zan iya ci ba" Kai ya gyada ya tayar da motar ya dauki hanyar gidansu da ita Bata ce komai ba, sai dai a zuciyarta ta ji dadin hakan dan ita kadai ta san irin kewar ahalinta da take yi, komai dadin gidan wasu gwara naka, dan a jiya an mata gata iya gata an hadata da wani luntsumemen gado da ac, ama zuciyarta sai ta ringa kwadayin inama ta samu yar katifarta da motsin ahalinta a kusa da ita? Dandai bata da yada zata yi da Hajia ne , kuma ko ba komai dan matsawar daga gidan ya taimaketa ainun dan ta samu zuciyarta ta dan saku da irin aibatatan da mutane suka ringa yi "Karfe bakwai zan dawo na daukeki na maidama matar cen ke " ya fada a hankali bayan ya tsaya a kofar gidan Murmushi ta yi ta bude motar ta fice da kwondon abincin dan a juyewa busashe ta wanke flsk din da aka zuba Sosai suka sha fira da Mama, Mama bata yi mata fadan da ta yi tunanin zata yi mata ba, saima rarashi da ta samu na ban mamaki da kuma ban baki Da kula Mama ta ce" Komai da kika gani na rayuwa mukadari ne, ban ce maki takurarwar mutane ba zata dameki ba dan kuwa hakan na iya damunki fiye da tunanin bawa, ama abinda na sani shine mu iyayenki zamu ci gaba da binki da addu'a har Allah ya fitar maki da miji na gari, Khausar a jiya Mujaheed ya zo da dare nema sosai , Abanku ya fita ya same shi, shin akoy wata matsala tsakaninki da shi ne da ban sani ba?" Khausar ta yi dan shiru gabanta na dan faduwa, a sanyaye ta girgizawa Mama kai Mama ta tabe baki ta ce" Kin san mahaifinki bai cika buden abu ba, a yadda dai na dan tsinci abin kamar ya fara kokonta a kan tarenku da mutumen , harma ya bashi damar ya fito idan da gaske yake, in ba haka ba kuwa ya yi hakuri kawai, ...........hakan ya sa na tsatsamci akoy abinda yake faruwa da baya birge abanku" Khausar ta yi tsuru gabanta na faduwa zuciyarta cike da tunanin ko wani abu ne ya faru? Mama ta ce" To ki kula, kafin komai mutuncinki ya fi komai a duniya, ki sani idan da rabon ki yi aure ko shekara nawa zaki dauka a duniya sunnanki mace , budurwa, kar ki yarda ko menene ya taba maki mutunci , kuma ko wani irin hargitsi ya tunkaro rayuwarki ki san cewa Allah ya haliceki shi ya dora maki ba kowa ba, ....., Sai maganar auren kannenki, a jiya fa iyayen wajen mijin rukaya sun nuna da wuri suke so, dan a cewarsu sati biyu, da kyar dai abanku ya tsaida abin nan da wata daya, kennan dole mu zauna mu yi shawara mu ga abinda zai fishemu ko?" Da mamaki ta ce" Ka8, da wuri haka Mama, na zatama sa kai bayan babar sallah?" Mama ta ce" Nima na zaci hakan, ama kin ga yadda Allah ya yi" Khausar ta yi murmushi ta yi addu'ar Allah ya nuna masu ranar da rai da lafiya Nan suka hade suka yi ta zantawa har baba ya dawo gida shima ya hadu da su ya ringa tsokanar Khausar yar gidan Hajia ya ce" Kin ga, TAUFEEK ya zo ya maidawa Hajia ke tun kafin ta tardoni tace ni na kwaceki" Dariya Mama ke yi ta kama baki ta ce" Ni ai jiya na sha dariya Ni kadai, Hajia fa hararena take yi wai ban san ciwon Khausar ba" Aba ya ce" Nima cewa ta yi ba sannin ciwon yar aka yi ba" Nan fa aka dauko caftar Hajia, Khausar ta ringa dariya dan walahi sai yanzu ta idasa sakewa har ta ji wasai a ranta, ta fada masu turaren da hajiar ta mata jiya da yau da safe, ai kam kannenta da iyayenta aka rasa mai ba dan uwansa hakuri dariya suke bilhaki, Aisha ta ce" Ni walahi tsoronta nake ji, idan tana fadan nan sai na ji kamar zata iya marina, kuma ita babu wanda ta bari, harta yaya TAUFEEK fa sai ku ji ta yanko shi , shi kuwa abin mamaki idan ya zura ido ya kalleta sai ka ga ya dauke kansa kamar Allah bai yi ruwanta ba, sam baya kulata" KHausar ta ce" Ke na rabaki da TAUFEEK, shi ai du lokacin da kake shirye ku yi balaki ne na zai biyaka ba, ki ga fa idan ina fushi da shi na yi na yi ya biye min sai kawai ya kare min kall9 ya dauke kai, ni kuwa hakan irin haushin da yake bani, sai in ga a banza kennan ban samu muka raba hali ba" Mama na dariya ta ce" To ai shi ba mashiririci bane da zai tsaya karamar yarinya ta fada ya fada" Haka suka yi ta sharfi sunna fara'a, a hankali kuma mutane na lekowa sunna sake yin barka da arziki da fatan Allah ya nuna masu ranar auren Zuwan TAUFEEK ya saka suka mike sukai mata rakiya, su uku, Aisha , Rukaya, da Auta har wajen motar A lokacin da ta bude ta shige a gaban idannuwanta yan zaman anguwar suke lekowa, ita kuwa ta cire kanta bata kula kowa ba ta shiga neman layin Mujaheed Sai da suka kusa isa gidan ya daga wayar, cikin dan basarwa ya ce" Batan numba aka yi ba?" Khausar ta yi dan murmushi a hankali ta ce" Barka da warhaka Elhaji" Elhaji Mujaheed ya amsata shima da kula Khausar ta ce" sai yanzu na ga misscall dinka, shine nace ko zaka iya zuwa nan gidan su TAUFEEK da yake a nan zan kwana? Idan har dare bai yi ba?" TAUFEEK dake tuki yana amsa waya ya dan kalleta kadan, sai kuma ya dauke kansa ya ci gaba da tukin Bai dai san me suka tatauna ba har suka karaso gida dan shi bai gama tasa wayar ba har sai da suka iso ya fice yana amsa wayar, ita kuma ta ciro kwanukan ta nufi bangaren Hajia da su Samu ta yi Hajiar bata nan, mai aikinta ta shaida mata tana bangaren su Mama, dan haka sai kawai ta shige bayi ta yi wanka ta fito ta cenza kayanta sannan ta zauna ta hada lipton mai zafi ta shiga sha a hankali tana dan duba agogo domin Elhaji Mujaheed yace ta bashi minti ashirin gayanan zuwa A lokacin da ya sanar mata yana cen babar kofa bai samu shigowa ba a dole ta mike ta shiga neman layin TAUFEEK, sai dai ta yi ta yi bai daga ba, gashi hajia bata dawo ba, abindama ya dan sakata kin bin hajiar da kuma kin zuwa ta gaisar da su mai aikin na hajiar cewa ta yi an zo an yi kiran hajiar ana fada a cen, hakan ya sa ta yi zamanta dan ba zata je kotai kotai bayan ta ji abinda aka fada ba Hijab ta saka ta Hajia dan ta nemi nata sama ko kasa ta rasa, da dan sauri ta nufi bangaren TAUFEEK tana sake gwada kiransa ama abin haushi ba'a daga ba A nutse ta dan buga kofar sannan ta kama ta murda da salama a bakinta Fara'a ce ta yawaita a fuskarta tana kallon Yumnah dake tsaye wajen diner, jikinta daure da rigar girki, hannayenta da safar sauke tukwane, tana sanye da wando da riga , wandon da kadan ya dan dara gwuiwarta , rigar kuwa mai siririn hannu ta juyo ta zubawa Khausar din ido ama kuma bata amsa salamar da ta mata ba A hankali Khausar ta dan dauke dubanta gannin yannayin shigar Yumnar tana dan murmushi ta ce" Matarmu, barka da dare, dan Allah ki yi hakuri na dame ki, ko freind na kusa?" Yumnah ta kare mata kallo, ta dago ta watsar sannan ta juya ta ci gaba da gyaran diner dinta ba tare da ta abata amsa ba Da dan mamaki Khausar ta dan juyo dan gannin ko dai bata bata jita bane?? *ALLAH BAI SAUKAR DA CIWO BA SAI DA YA SAUKAR DA MAGANINSA* Ni ce dai Fareeda Abdallah, na sake dawo muku da tallen magungunanmu da zuwa yanzu bazan iya ƙayyade yawan waɗanda suka dace da biyan buƙata sanadiyyar amfani da maganinmu ba. Alhamdulillah! Ƴar'uwa ki gwada, wataƙila warakarki na tattare da maganinmu. Haihuwa ce baki taɓa yi ba ko kuwa jinkiri kike samu sanadiyyar planning ko kuma haka kawai? Muna da ingantaccen maganin rashin haihuwa ga mace da namiji, wanda za ki bada sadakar 2k ga matsalar ko wane ɓangare. In sha Allah za ki dawo da godiyarki bayan amfani da maganinmu. Sanyi (infection) ne yayi miki yawa yake saka ki ciwon mara, zubar farin ruwa, ƙaiƙayi, ƙuraje, ɗauke ni'ima, har ma ya saka mijinki ya dinga miki gani-gani saboda bakya gamsar da shi? Da naira 3k zamu haɗa miki magungunan da za kisha ke da Oga in dai kika yi amfani da su ku da sanyi har abada in Allah ya yarda. Muna sayar da ingantaccen haɗin sabaya, wanda zai sa nonuwanki su cicciko, hatta fatar jikinki sai ta murje sanadiyyar shan kunun sabayarmu. 2500 bokiti 1litter. Muna da maganin wankin nono ga mai ciki da mai shayarwa, wanda indai kikai amfani da shi yaronki zaiyi tubarakallah, ba ruwanki da laulayi. Muna da ingantaccen maganin Daji (Cancer), typhoid, maleria, yaron da yayi nauyin ƙafa, da sauran cututtukan da ban ambata ba. Muna aika maganinmu ko ina tsakanin Nijar da Nigeria, ga masu buƙatar magani da gaske su tuntuɓeni akan lambar wayata 07039080978, ko 09077591726 Noted: *MAI SON MAGANINMU IDAN BA A KADUNA YAKE BA, SHI ZAI YI KUDIN MOTARSA HAR ZUWA INDA YAKE, BABU INDA BAMA TURAWA IN SHA ALLAH.....SAI KUN ZO* 💔💔💔💔❤‍🩹❤‍🩹💔💔💔💔 *DA CIWO A ZUCIYATA* 💔💔💔💔❤‍🩹❤‍🩹💔💔💔💔 _MALLAKIN_ *SAJIDA NIJAR* *FREE BOOK NE* 2️⃣3️⃣ LITATAFAN MARUBUCIYAR Duk karyar kada Yar mahaukaciya Neman na kaina Bani da zabi Bak'a ce Kutkale Makauniya ce Mage Duk nisan jifa Idan ka raina inda kake Dutse Alkalamin kadarata Bani da zabi Dakika Biyar Now *Da CIWO A ZUCIYATA* *Tallah, tallah, tallah* *SECRET DE LA FEMME DU MANGA* _Gidan Kamshi, Sirrin Manyan Mata, nesa tazo kusa,Amarya ,Uwar gida,Ango da mai gida Har ma da yan mata da samari shin kuna sane da cewa HAJIYA FUSAM ta shirya tsaf domin gwangwaje ku da turarakunta masu dankaran kamshi? Tare Kayan gyaram jiki na musamman ,wanda daga nesa kamshin ki kadai ya wadatar ya isar da sakon zuwanki waje,gidan ki kuwa sai ya zam abun kwatance wajen kamshi, kar na cika ku da surutu bara in fara zayyano su_ Farar Humura Bakar Humura Humura special, humura de bain Humura epicé Lait de nuit Parfums désodorisant Parfums rideau et dras Lait de nuit Alkam Kulakcam *Waɗannan kadan ne daga bangaren turaran ruwa* Gagab, sandal flex, Durot, durus, sandal fleur, tafarce, farce, sandal bangui, sandal, hypotonic sandal, al'ut, coktail creation VIP, Gajiji, Mankaji, turaran wutar labule da cafet, Aba malan, boulettes *Munada bangaren gyaran jiki kamar haka:* mai mai saka santsin jiki, mai mai kanshi, Kayan gyaran jiki mai saka fata ta yi santsi da laushi, kayan gyaran jiki mai saka fata ta yi fari, Sabulu mai saka fata ta yi haske, sabulu mai saka fata ta yi santsi, sabulu mai goge yanayin fata, mai wanda baya saka fari mai gyara fata Sayen na gari mai da kudi gida,sai an gwada akan san na kwarai💃💃 Hajiya Fusam na zaune a kasar Niger domin yin magana da ita kai tsaye tuntuɓi wannan number 97 82 44 94 *SECRET DE LA FEMME DU MANGA* Gidan Kamshi, Sirrin Manyan Mata💃💃💃💃💃 Da dan Mamaki Khausar ta juyo dan gannin ko dai bata jita bane?, Sai ta ga aikinta take yi bata kuma bi ta kanta ba Da wani mamakin ta dan sake dubanta, sai ta dan koma baya ta sake yin salama wannan karron da dan karfi Sai dai abin mamaki bata ajiye maganarta ba ta ga Yumnah ta yi wani ecpression da fuskarta sannan ta dan ja tsakin da sarai ta ji shi ta saki abin zuba abincin dake hannunta ta juyo tana cire safar hannun nata ta dangwarar a nan da wani yannayi irin na wulakancin nan dake bayane ba a boye ba ta ce" Na ji ki, ban san inda yake bane" Daga haka ta juya da saurin tafiya ta koma kicin Baki da hanci ke bude Khausar ta rakata da kallo har bata ji takun saukowarsa ba sai muryarsa da ta ji ya ambaci sunnanta yana idasa saukowa da mamakin ganninta dashe a nan baki bude A dan tsorace ta juyo da madaukakakin mamakin da bai barta ba ta zuba masa ido, sai kuma ta dauke dubanta a kansa na tsarewa da kallo, domin farar riga ce a jikinsa ama botiranta a bale sai ash color din snglt a ciki mai siraran hannu , hakan ya dan bayana wasu sashe na sirrin jikinsa wanda bata taba ganni haka kai tsaye ba Hannunta na dama ta saka tana dan murza goshinta cike da shiga rudu da kuma yar kunyar yannayinsa ta dan juya ta ce" Am, barka da yanzu, dama ina kiranka ne baka daga ba sai na zo , Mujaheed ne ke cen kofa nake so idan ba damuwa a shigo da shi ko a fada masu na leka ......???" Ta idasa maganar tana dan ajiye zancen da dan sake duban hanyar kicin din nan "Ok" kadai ta iya ji daga bakinsa, sai kuma ta ji yana magana da waya cewar a bar bako ya shigo a nan kofar gidan A hankali ta dan juyo dan yi masa salama, sai ta ga ya bala boturan, hakan ya sa ta samu sakewa ta dan dube shi ta bi wayar dake hannunsa da kallo, wace ta tabata itace mai dauke da numbar da ta yi ta kira tun dazun bai daga ba, ta so kwari yi masa korafin hakan, sai dai wani abu da ya dan tsaye mata a kahin zuci na yannayin da matarsa ta yi yanzun ya dauke hankalinta, a hankali ta juya ta ce" Thank you" sannan ta yi waje Kansa ya mayar a zaunen da yake jikin kujerar ya lumshe idnanuwansa Shin ta ina zai bi ya raba wannan alaka? Barin wannan alaka dan ta ji dadi anya daidai ne? Idan ya yi duba da tarin abinda ya sani shi a kan manemin auren aminiyarsa kuma kanwarsa in ya yi shiru ya yi mata adalci daga ita har iyayenta kuwa? Shi dai ba abikin yin Mujaheed bane, abinda ke iya sab hanyarsa da tasa daya ce tak idan shagonsu na son sari a kampani, bayan wannan babu ta inda wani abu zai iya hada su, da ya dan kwatanta ganninsa sun zanta a kan lamarin......, A gaskiya baya tunanin in har zai iya yin hakuri ya zuba ido KHAUSAR ta auri mutun irin wannan bayan du irin wahalar da ta sha ta rayuwa a kan wannan subjet na mijin aure ba Kwata kwata shi din ba mijin mace irinta bane Ba dan aljihunsa ba ko yannayinsa ba, sai dan Halayarsa da suke boye wajen yan mata ama suke bayane wajen wa'inda suke iya sani "Honey, na kawo abincin nan ne?" Yumnah ta katse tunaninsa da sanyayar muryarta da yannayi irin na macen dake gabar son birge abin birgewarta Idannuwansa ya lumshe a kanta , sai kuma ya mike yana dubanta ya ce" Ina zuwa Yumnah" Daga haka ya nufi hanyar fita a falon Da ido ta bi shi, kirjinta na dokawa da tunanin ta yiwu wancen abar zai bi? A hankali ta silale saman kujera ta dafe gaban goshinta da hannayenta bibiyu tana tunani, tunani take yi anya kuwa tana cikin hanyyar da zata kubuta daga wannan mugun abin dake faruwa a aurenta? Duka duka yaushe aka yi auren ama ita ta hadu da kalubalan zaman auren fiye da tunanin mai karatu, babu lokaci idan wannan mata ta nemi layin mijinta yana iya amsawa, babu lokaci idan ka ganshi kana iya ganninsu tare, ba dangin iya ba na Aba an kwaso katuwar mace an kawo gidan da mijinta yake da ta dan nuna sai ya nuna tamkar yar uwarsa yake kallonta? Anya ba zata yi tashi irin na kirki dan gannin ta samarwa kanta mafita daga wannan abin ba? .....da wannan bacin ran ta yi zamanta a nan tana neman mafita da tunaninta Fitar da ya yi shi kuwa bangaren iyayensa ya nufa , domin tunda ya zo bai shiga ba, ashe rabon ya tarda abinda yake faruwa ne, rikici tsakanin iyayen nasu , Hajia na zaune tana ta kashe wuta tana fada domin mahaifinsa baya nan A hankali ya fice a falon, ba dan komai ba sai dan gannin halin da suke ciki, ya tabata in dai yace zai zauna to yana iya haduwa da bacin ran da zai saka ya kasa hakuri Sometimes, yakan ji kamar ya dauki mahaifiyarsa ya kaita nesa da wannan rayuwa, ama idan sun kadaice sai ta ringa kwatanta masa cewa wannan din ba damuwarsa bane tsakaninta ne da matan mahaifinsa, ya barta zata iya kwatar kanta tunda ita ba yarinya bace, kuma zaman aure take yi dole zatana haduwa da kalubale na yau da gobe, shi dai ya ci gaba da addu'a ya kuma kiyaye huldarsa ta yai da gobe da kowama A bangaren Khausar Tunda ta shiga motar bayan ya nuna mata cewa in bata shigo ba a ina zasu zanta? Duba da bata kawo masa kujera ba kuma bai ga wajen zama ba, kanta ke kasa tana sauraron irin tarin mitar dake bakinsa da kuma rikicin dake cikin bakinsa Gaba daya rigimarsa idan ya jema ya dawo a kan TAUFEEK take sauka, hakan sai yake bata mamaki, ama ta nutsar da tunanintaa tunawa da wasu kalaman da ta ringa haduwa da su cewa dole fa zata iya haduwa da haka, ba kowaki namiji bane zai yi hakuri da mu'amala irin wannan dan haka a sanyaye yau ta budi baki bayan ta dago ta masa duba kamar sau biyu ta ce" Na san ba zaka taba yarda cewa mu'amalata da TAUFEEK zumunci ne kawai ba Elhaji, ka sani zumuncina da shi ya hada zumunci da iyayenmu, ko yanzu da ka ganni a gidansu Hajia ce ta zo da ni, a bangarenta nake kwana ina tashi, bayan wannan Elhaji maganar mu'amalata da TAUFEEK a yanzu da nake budurwa take da karfi, idan na yi aure du abinda mijina ya shinfida min ai dole zan yi biyaya in dai hakan bai sabawa adinina ba, dan Allah ka yi hakuri ka cire wannan magana daga ranka kwata kwata" Har ga Allah, bai taba jin salama a maganarsu kan TAUFEEK ba irin nna furucinta na yau, ko dan ya kasance mutun mai son a girmama shi? A yanzu yana jin zai iya tunakarar wannan masifafiyar matar da ya kakabowa kansa take neman hanna masa rawar gaban hantsi, mace sai fitina, mace sai neman fitina, yanzu abinda ya fi jin tsoro maganar nan, da ya kwatanta ashariyar da ta dura a kan yarsa sai da cikinsa ya juya, ama abu daya ya sani ita din mayar kudi ce, zai kwatanta lasa mata zuma ya san da wahala ta iya kin amincewa da maganar auren nan, shi fa har mafarkin Khausar yake gashi ga ita matsayin matar aure, kuma ya tabata da wahala matarsa ta fi karfin Khausar dan kuwa in me take takama a jikinta Khausar ta damata ta shanye "Mun yi magana da Aba, Aba ya nunan bacin ransa dan na je jiya da jus, yace baya son haka kar na kuma, sannan ya min maganar na fito idan da gaske nake" Ya fada yana dubanta Khausar ta dan dago ta dubeshi sau daya ta sake dauke dubanta a kansa, a ranta tana tunanin yauwa ga abinda ya hasala Aba, dan ya masa magana ba sau daya ba, ba sau biyu ba, ama shi kamar baya jin me ake nufi da kar ya yi Ya dan sake muzgutawa irin rikakun mazan nan da suka isa da gidansu ya ce" in sha Allah karshen watan nan za'a kawo sadakina, shikenan zaki zama tawa ko Khausar?" Khausar ta sake sada kanta, tana jin wani abu na dan ratsa zuciyarta mai shige da salama A hankali ta ringa jin kamar wani abu mai kama da kwonciyar hankali da nutsuwa na game zuciyarta, har dan murmushi ya wanzu a saman fuskarta ta yi gagawar rufe fuskar cike da jin kunya Hakan ya sa ya sakota a gaba da zolaya dan ya riga ya sani Khausar akoy kunya kamar me Da wannan ta masa salama ta koma ciki, shi kuwa ya juya ya tafi daga gidan yana sake kallon gidan da gyada kai, shi da kansa ya san nan ana magana ne ta babansa ba wai yayansa bama a dukiyar, zai yi gagawar dauke matar nan ko dan ya ringa fada a cikin maza cewa ya yiwa ELHAJ TAUFEEK kwacen mace..... Da Khausar ta koma bangaren Hajia ta tarda ita zaune saman kujera da waya a kange a kunnenta Zama ta yi bayan ta cire hijabin na Hajiar a kasa daf da Kafar Hajiar ta dan kamo kafar tata ta shiga matsa mata a hankali a hankali Jim kadan Hajia ta gama wayar ta dubeta da murmushi tana amsa gaisuwarta kafin ta ce" Kin zo bana nan, da na dawo kuma sai wancen yar tace kin yi bako, wanene ne ?" Khausar ta sada kanta tana dan murmushi ta ce" Hajia, wanda yake zuwa wajena ne " Hajia ta dan yi shiru tana kallonta, a hankali ta ce" A ina yake, menene sana'arsa? Saurayi ne ko magidanci?" Khausar ta dan sauke numfashi a ranta ta ayana' To Fa Allah ya sa kar a koreni dan haushina' A nutse ta sanarwa Hajia amsar Tambayoyinta Hajia ta dan tabe baki tana fadin" Ni fa ban cika son namiji mai kai kawo ba kamar mace, to me yake jira da bai fito ba? In fa baya yi karma ya nemi bata maki lokaci a banza a wofi, gwara ya gusa wani ya shigo!" Khausar dai kasa cewa komai ta yi, Hajia ta janye kafarta da kula ta ce" Tashi ki je bangaren iyayenki, in kin samu wani a falo ki gaishe shi ki haye sama wajen Mamanku tana kiranki" Mikewa Khausar ta yi ta dauki hijabin ta saka sannan ta tafi Da kallo Hajia ta rakata kafin ta dauke dubanta ta dan sake lumshe idannuwanta tana ci gaba da jan carbinta Sai dai a kasam zuciyyarta wani abu ke damunta ainun dangane da matan yaron nata, akoy wasu furuci da ta tsinta a yau din da suka tsaye mata a kahon zuka, sun mata bake bake har sunna son hannata wani abin cikin walwala, Ita dai yar hausa ce bata cika daukan magana a shantakai ba, magana kuwa irin ta gannin baya bata cika sonta ba, shi yasa ta shiga a hali na tunanin shin zafin kishi ke damun matar ko harda matsala wata daban?...... (Wannan kennan) Khausar jiki ba laka ta karasa dakin Maman TAUFEEK , sakamakon irin amsa gaisuwarta da mutanen nan suka yi a lokacin da ta shigo da yar fara'arta Ta samu Maman TAUFEEK din saman salaya ama kuma ba sallah take yi ba, tana dai jan carbi ne Da fara'a sosai a saman fuskarta take amsa gaisuwarta sannnan ta mata nuni da wajen zama ta karasa adu'arta ta shafa ta juyo fuskarta a sake ainun ta ce" Khausar yaya bakunta ya fama da kakar taki?" Khausar ta yi yar dariya ta ce" Alhamdulilah Mama" Mama ta mike tana nufar wajen wrdrb dinta ta bude tana fitar da wasu manya manyan ledoji masu dauke da sunnan wani rantsatsan kampani da ake yayi a garin masu kawo lesuka da atampa da shada da kuma abayoyi ne su mayafai dai da sauransu Ajiye su ta yi nan bakin gado d taimakon Khausar sannan ta shuga fitar da su da kula ta ce" Na cewa aminin naki gobe ba zaki je asibiti ba dan ina so mu fita, ya so ma ya kiya dai na fada masa ba fa zaki je ba ya sanar masu dan zamu je wajen mai dinki da kuma shagon Hajia FUSAM mai turaren wuta" Maganar cewa ya sanar ba zata je ba ta so ta dan sakata a tunani, sai dai maganar sako sunnan FUSAM ya cire mata tunanin da dan mamaki tana bin rantsatsun atampopi da lesukan da Maman ke fitarwa da kallo ta ce" Lah Mama kin san Fusam kennan?" Mama ta yi murmushi ta ce" na san Fusam Daughter ai wajenta nake siyan turarukana, yaya kika ga lesukan nan sun birgeki kuwa?" Nan fa ta ringa shafawa tana fadin cewa babu na yarwa baki daya sun tafi da ita tun daga yannayinsu da color dinsu a kalla sun kai goma ko fi dan ba irgawa ta yi ba ama kuma sun rikitata Itama Maman ta ji dadin haka, dan haka ta umarceta kan ta je da su bangaren Hajiar gobe sai su kai dinki in sha Allah, harda dorawa da fadin a ciki abinda bai mata ba sai a cenzo mata dan a online ne ne ta yi siyayar Mamaki, tsoro, rasa abin cewa ya saka Khausar sake tambayar Mama wai tana nufin nata ne? Mama ta gyada kai tana mayar da su ciki harda mayafan yan yololuwai da su domin shara shara ne ama rantsatsu irin na yan gayun nan yan mata Gaba daya sai Khausar ta rasa abun cewa, ta rasa me zata ce, ta rasa ta inda zata yiwa Mama godiya, ta gaza zaune ta gaza tsaye har sai da Maman ta nuna mata bafa ta son haka ta yi addu'a kawai ta yi shiru ita yarta ce dan ta mata alkhairi ba wani abu bane Da zumudin wannan ta koma bangaren Hajia, nan fa Hajia ta saku daga yannayin da take ta ringa shiwa Mama albarka kamar irin an yiwa bakuwarta alkhairin nan, sosai ta ringa sakawa Mama albarka bama da ta ji cewa zasu je wajen dinki da sauransu a goben, da wannan farin cikin suka kwonta barci Washe gari kusan karfe tara na safe tana tsakar gida ta dora tukunya saman murhu tana tukawa Hajia tuwo na masara da tace tana sha'awa ta ajiye karamar kujera ta yi zama irin na tuka tuwon domin ko hijab bata da shi , haka kuma ta nanade zanin jikinta ya dan yi sama kadan ta yi zaman nan na gantsarewa kadan tana dirkar tukin tuwon mai aikin Hajia na gefe tana mamakin Khausar din domin bata san cewa ta iya tuka tuwo haka ba Salamar Hajiar wace ta fita tun da sasafe ita da Magidanci ne ya saka Khausar dan dagowa tana amsawa hadi da fadin" Hajia har kun dawo?......" Sai kuma ta yi shiru sanadiyar gannin TAUFEEK ya shigo da waya a kunnensa shi sarkin amsa waya sai ky a hannunsa yana dan yiwa hajia Alamun ta tsaya dan juyawa zai yi kasuwa Ido hudun da suka yi da ita da shi ya saka shi binta da kallo sakamakon hayakin da yake ganni na tashi a gabanta, nan idannuwansa suka yi arba da irin zaman da yarinyar nan ta yi rabi da rabin cinyoyinta du sun sauka daga marainiyar kujerar nan ta nade hannun riga ta wani yada zama kamar an mata gorin haka tana tuka tuwon da bai san wa ya sakata aikinsa ba Cire kansa ya yi ya maida kan Hajia zai yi magana, sai ya ga Hajia tana wani rinrintse ido tana wani tabo baki tamkar ba daga wajen rasuwa ta fito yanzun ba tana rus kuka har ana bata hakuri kamar jikanta ne ya rasu wato shi Ido ya kifta a sanyaye yana kallon yannayin Hajiar, dan a gaskiya in dai Hajia wani abin ta saka a ranta yau zai fito mata a mutun ya mata nasiha Kasa kasa hajiar ta matso har tana dan dage ta ce" 💔💔💔💔❤‍🩹❤‍🩹💔💔💔💔 *DA CIWO A ZUCIYATA* 💔💔💔💔❤‍🩹❤‍🩹💔💔💔💔 _MALLAKIN_ *SAJIDA NIJAR* *FREE BOOK NE* 2️⃣4️⃣ LITATAFAN MARUBUCIYAR Duk karyar kada Yar mahaukaciya Neman na kaina Bani da zabi Bak'a ce Kutkale Makauniya ce Mage Duk nisan jifa Idan ka raina inda kake Dutse Alkalamin kadarata Bani da zabi Dakika Biyar Now *Da CIWO A ZUCIYATA* *Tallah, tallah, tallah* *SECRET DE LA FEMME DU MANGA* _Gidan Kamshi, Sirrin Manyan Mata, nesa tazo kusa,Amarya ,Uwar gida,Ango da mai gida Har ma da yan mata da samari shin kuna sane da cewa HAJIYA FUSAM ta shirya tsaf domin gwangwaje ku da turarakunta masu dankaran kamshi? Tare Kayan gyaram jiki na musamman ,wanda daga nesa kamshin ki kadai ya wadatar ya isar da sakon zuwanki waje,gidan ki kuwa sai ya zam abun kwatance wajen kamshi, kar na cika ku da surutu bara in fara zayyano su_ Farar Humura Bakar Humura Humura special, humura de bain Humura epicé Lait de nuit Parfums désodorisant Parfums rideau et dras Lait de nuit Alkam Kulakcam *Waɗannan kadan ne daga bangaren turaran ruwa* Gagab, sandal flex, Durot, durus, sandal fleur, tafarce, farce, sandal bangui, sandal, hypotonic sandal, al'ut, coktail creation VIP, Gajiji, Mankaji, turaran wutar labule da cafet, Aba malan, boulettes *Munada bangaren gyaran jiki kamar haka:* mai mai saka santsin jiki, mai mai kanshi, Kayan gyaran jiki mai saka fata ta yi santsi da laushi, kayan gyaran jiki mai saka fata ta yi fari, Sabulu mai saka fata ta yi haske, sabulu mai saka fata ta yi santsi, sabulu mai goge yanayin fata, mai wanda baya saka fari mai gyara fata Sayen na gari mai da kudi gida,sai an gwada akan san na kwarai💃💃 Hajiya Fusam na zaune a kasar Niger domin yin magana da ita kai tsaye tuntuɓi wannan number 97 82 44 94 *SECRET DE LA FEMME DU MANGA* Gidan Kamshi, Sirrin Manyan Mata💃💃💃💃💃 Kasa kasa Hajiar ta matso har tana dan dage ta ce" Ka ga mata, wannan sunne mata, irin matan da na so ace ka wanko ka kawo min, wa'inda na san du gajiyar da ka kwaso to fa kana da wajen saukewa, magidanci irin matan nan ina iya rantse maka idan suka rike namiji an gama, ama sai ka je ka dauko mace gatacen sai shegen shafa pankeke, yo in yar nan ta yarda ta koyi shafa pankeke ai an kade, ina mana bakin cikin rasata Allah ma kuwa!" Gata dai fuska du ta fara nuna alamun daf take da zagwonyewa dan tsufa, ama bakinta ko amon muryarta bai cenza ba, shi a yau in ba dan mai kwanoni ba da matar nan sai ya saka an zo an ririketa an sauke mata aljannun kanta, ama ba komai zai kyaleta ne har su tafi haji shi ya san yaya zai yi da ita Banza ya mata ya juya zai bar gidan, Hajia ta daga murya ta ce" Au na bata maka rai Hala dan nace wancen abar kamar muciya? Na fada in ranka ya kiya ka kawo mace mai dima dima mana ka gani in an zageka dilla malan" A hankali Khausar dake rage wutar nan ta dan dago ta kalli Hajia, an yi katari itama ta kallota sai ta karaso tana sakin murmushi ta ce" Yar nan tuki ake? Sannu ke kuwa tashi ki yi wanka ku tafi mana tace karfe goma zaku tafi fa, tashi maza dan watsa ki dan sha na sha kin ga na karbo maki wani na farin jinnin yanzunnan wajen malan, je ki yi wanka kafin ki fito na saka maki a nono sai ki sha " Khausar ta amsa hajia da to, domin bata da amsar da ta wuce wannan ta mike ta je dan shiryawar ta barawa mai aikin Hajiar sauran aikin, Tana gama shiryawa ta dauki wayarta da nufin kiran TAUFEEK, dan ta ji yaya maganar wajen aiki ne yau? Kamar yadda Mama tace shin yana da hanyar da zai sanar masu ba tare da an mata fadan rashin zuwan ba, sai kuma ta dakata da wayar a hannunta tana tuna abinda ya faru jiya, ko yau ba wani gaisuwar da suka saba suka yi ba dan sai take jin wani iri a cen kasan zuciyarta da tarin tunanin me hakan ke nufi, sun dai gaisa da murmushi ama bata wani tsaya ta ji daga gareshi ko ta masa tambayar iyali ba Salama ta yiwa Hajia ta wuce bangaren su Maman bayan hajiar ta shaida mata ta bar kayan za'a mika mota Yau dinma sai da aka bata damar shiga kafin ta shiga baban falon Mutanen dake falon ta fara bi da kallo kafin ta gaishe su, sai dai a cikinsu yar budurwa matashiya daya ta amsata itama a dan fizge ta dauke kanta Ido ta zubawa Yumnah gannin sai da ta dubeta ta watsar Tana shirin hawa saman sai ga Maman na saukowa da yar karamar jakkar hannu Yumnah ce ta fara mikewa tana dan sosa gaban goshinta alamu na dan jin kunyar surukar nan ta shiga gaisar da Mama Da dan sauri Maman ta amsa ta karasa saukowa ta dan dube su baki daya ta ce " Barkarku da hutawa, zamu dan fita ne da Khausar sai mun dawo" Hajia Nuwairah ta yi kamar bata jita ba sai yarinyar wajenta da take riko wato hamdiya ce ta karasa da dan sauri tana sake gaisar da Maman Jakar hannunta da Hamdiya ta so karba Maman ta dan rike da kula sosai tana mata murmushi ta ce" Na gode yata yi zamanki ai ba wani nauyi Allah ya maki albarka" Hamdiya ta amsa tana dan sinne kai irin girmamawar nan tana kuma.jin dadin adu'ar Maman a ranta, a cen kasan zuciyarta kuwa ba abunda ke faranta mata a yanzu irin ta faranta ran yayansu ta hanyar yin abinda Yayansu ke so Mama kuwa daga haka ta fice tare da KHAUSAR suka yi tafiyarsu Cike da isa irin tata Hajia Nuwairah ta dan sake kallon yannayin Yumnah, sai kuma ta saki dan murmushi tana dauke dubanta cikin basarwa ta ce" Ya haka Yumnah na zata tare ne zaku fita da srakuwar taki?" Yumnah ta juyo da dan sauri, dan kamarma wace ta afka tunani ta kalli Hajia Nuwairah, sai ta ga hankalinta ba a kanta yake gana daya ba, tana dan yi nata firar ne kuma tana maida hankali kan Hamdiya Dan numfashi ta fitar, sai kuma ta juya tana fadin" Bara na koma Hajia dama gaishe da ku na leko" Daga haka ta yi gaba Tan fita Hajia Nuwairah ta mike ta kama kunnen Hamdiya ta ja da karfi ta yi wajen kicin dinta da ita danma kar a fito a sameta da ita a haka Rai bace tana rike da kunnenta ta ce" Ke na tambayeki, Hajia fatima kanwar uwarki ce?" Da sauri Hamdiya ke girgiza kai tana ji kamar Hajiar zata tsinke mata kunne ne Murya a kausashe ta ce" To ki kula, bana son rainin hankali da shishigin tsiya, ba abinda ya hadaki da ita, ko gaisuwar kirki na ga kin kuma yi mata sai na wulakantaki sannan na maida ke gidan ubanki, dan ba zai yiwu ba na dauko ki na kawo ki kashe ni kina shiga gindin kishiyata da ba kaunata take yi ba, ke shaida ce a gidan nan dan ta haifi namiji daya kwal ba irin abinda ba'a mana a kanta da danta, to ba zai yiwu ku da kuke nawa ta kwace min ba kin fahimta?" Kai take gyadawa har idannuwanta sun cika da kwala kafin ta saketa ta fita da sauri ta haura sama ita kuwa Hajiar ta ja tsaki tana sake hade fuska domin abin ya bata haushi ainun, sai dai wata hanyar da ta hango ta baraka ta sanyaya mata zuciya, domin ta tabata in dai har abinda ta gani a idannuwan Yumnah kishin wancen yarinyar ne to fa zata bi ta nan ta sa rashin jituwa tsakanin Hajiar da Yumnah, tana ji tana gani sarakuwar ɗan nata sai dai ta hangota ba dai su yi wata taraya ta zumunci ko fahimtar junna ba! Sosai Khausar ta ji dadin fitar nan, sun je an aunata, daga nan suka je Hajia ta daukar mata takalma masu kyan gaske harda kafa ciki mai dan karamin hls a jikinsa fari kal mai kyan gaske, harfa kayan kwaliya, daga nan suka wuce wajen HAJUA FUSAM, nan fa ta sha kallo ta nemi rikicewa har ta ji wani irin sha'awar son ta ringa gyara jikinta irin na matar da kayan aikin matar, lalle mata sunna gyara, tun daga su dilka, kurkum, kujera, rigar dilka, itacen dilka, turare kai komai da komai dai a wajen matar nan akoy masu kyau da inganci , turatukan da Mama ta daukar mata sai da ta ji kamar ta bude ta yi ta sinsina a hancinta, turaruka masu kanshi , sanyin kanshi da saka nutsuwa a zuciya, daga nan suka wuce gidan aminiyar Maman , nanma sakonta ta amsa sannan suka wuce gidan su KHausar din dan Maman ta yiwa Maman su KHausar din barka da abin arziki, nan ta shaida mata an saka ranar ance nan da wata daya sannan ta ringa godiya dan Khausar ta kasa r8ke murnarta ta sanarwa Maman komai da komai , har maman ta rasa abin fada , sun jima sunna zantawa kafin su tafi gida Da wannan Khausar ta karra kusan sati a gidan su TAUFEEK, a kulun zata je wajen aikinta ta dawo ne, kuma a kulun din shine zai ajiyeta ya je ya daukota, ko fushi fushin da ta so masa na yannayin matarsa sharewa ta yi ta daukarwa kanta alkawarin zata gane me hakan ke nufi dan ta dauki mataki, Yumnah dai ba sa'arta bace ba sa'ar yinta bace, ko tana da wata matsala da itane bata sani ba zata bi a hankali idan ta gane sai ta magance in mai magantuwa ce, in kuwa ba mai magantuwa bace sai ta kama kanta, dan ba zata taba yarda wani abu na rashin da'a ya shiga tsakaninta da ita ba, bata ga dalili ba Ranar da zata koma gida sai da ta ji ba dadi a ranta, Hajia fadi take ta yi zamanta mana, itama ta yi sabo da ita harda na mamaki, dan Khausar akoy dadin zama ga girmama manya ga rashin kiywa, da kyar dai ta iya tafia bayan an cika boot da tsarabe tsarabe da dinkunnanta da kayayakinta tamkar wace ta je wata kasar ta shekare, Mama kuwa ta sakata daki ta mata nasiha mai kama da fada fada, ta yi mata nuni kan yafa dace ta dan gyara, sosai ta hadata da mutanen arzikin da zasu sake gogar da ita a hanya mai kyau ba lalataciya ba, irin tarayar nan da koda baka son gyarawa idan ka yi tsai ka ga yadda mutane ke gyarawar kaima sai ka tsinci kanka a ciki tsamo tsamo A lokacin da ya ajiyeta gida murna wajen yan uwanta ba'a magana Haka su mama ke saka albarka a tarin arzikin da ta dawo da shi, yan anguwa kuwa sunna leke da zunde da bakinsu da mamakin inda ta je har ta jima haka, Ko da Baba ya dawo shima farin ciki kamar me, kasa boyewa ya yi, nan ta nuna zata raraba kayan da yan uwanta Baba kuwa ya nuna aa ko daya summa ai ga sababin kaya nan na aure ta ajiye abinta itama ta ringa sakawa Haka baba ke daga yan jakunkunnan da takalma yana fadin" Ai zaki saka ko khausar din Aba?" Ita kuma tana dariya da fadin" Baba bara ka gani zan saka duka kaffff, kuma harda kwali" Ita dai Mama dariya take yi a ranta tana ayana' Allah ya sa Khausar din ta saka" Kwonci tashi har lokacin auren yan uwanta ya karaso, aka sha biki har biki dan kuwa an yi taro yan uwa da aminan arziki haka yan anguwa sun yi karra sosai an samu tarin gudunmuwa harda na mamaki, dama Aba bai yi sanya ba ya masu abinda ya dace daidai karfinsa haka kuma an ci an sha da anki din atampa daya da suka fitar har dare ya yi aka raka kowace dakinta, ya zamto a gidan a yanzu Khausar ta sake tsintar kanta daga ita sai ita domin Auta namiji ne kuma bama dakinsu daya ba, shi dakin Aba yake kwana Wannan sabon kadaici ya so ya dameta sosai, dan kuwa har sai da Mama ta yi da gaske sannan ta dan saku, ba dan ta warware ta cire komai a rai ba, sai dan irga yan kwanakin da take tunanin itana tana iya wayar gari da sunnan amarya dan kuwa a irgenta kwana duka duka hudu ya rage alkawarin Mujaheed da ya mata cewar za'a kawo sadakinta Sai dai shiru, Aba bai yi mata zancen an tuntubeshi kan maganar ba, ko aiki da take zuwa kuzarinta ragage ne, duda an kusa yayeta dan a yanzu ta haura wata biyu cikin na ukunta take, aiki ta koye shi daidai gwargwado, ama kuzari ya ragu a jikinta saboda tunani da neman mafita a cen kasan zuciyarta Ba sai an fada mata ba, damuwar iyayenta a duniya a yanzun itace Ba sai sun tsangwameta ko sun hannata zaman lafiya ba, ta kalli fuskarsu su kalli tata du safiya ta Allah a matsayinta da shekarunta sun isa su dami kwakwaluwarta da kwonciyar hankalinta Wannan dalilin ya sa koda yaushe wayarta a hannunta take, kunnenta kuwa na sauraro dan son jin sauti daga gare shi, sai dai kwana biyu na ragewa watan ya cika sai ta neme shi dif ta rasa, domin kiran da yake mata na sasafe da darenma idan ba zai zo ba sai ta nema ta rasa Sannu a hankali kwanakin da take irgawa suka shige, nan fa abin ya fara bayana a jikinta domin nan da nan ta fara neman fita a hayacinta, bata fahimtar komai har sai da aka bata kwana biyu a wajen aiki a tunaninsu bata da lafiya ne Wannan damuwa tata ta saka Mama a damuwa har ta tirketa ta ji dalilin rashin cin abincinta da yawan tunaninta Jin abinda yake faruwa ya saka Mama ranta ya baci, a gaskiya abin nan ya fara kona mata rai, ita da kanta a irgenta sau uku kennan Mujaheed yana fadin yau gobe, dan haka ta samu Aba da maganar ta sanar masa Su dukansu basu zaci cewa Fada Aba zai rufesu da shi ba sai da ta fada din, ta inda yake shiga ba ta nan yake fita ba, cewarsa in har ya yi niya ya shirya to ya fito din in kuwa bai fito ba ba lalle ba dole shi baya neman rabuwa karfi da yaji da yarsa, kuma ya amshi kadararsa ko wace iri ce!, Bacin ran wannan ya saka shi ficewa ya bar masu gidan tunda duku duku ya ki dawowa Sun wuni cikin tashin hankalin nan wani ya sake samunsu, domin kusan karfe hudu na yama aka yi salama cewar ta yi bako ana mata magana a kofar gida............. 💔💔💔💔❤‍🩹❤‍🩹💔💔💔💔 *DA CIWO A ZUCIYATA* 💔💔💔💔❤‍🩹❤‍🩹💔💔💔💔 _MALLAKIN_ *SAJIDA NIJAR* *FREE BOOK NE* 2️⃣5️⃣ LITATAFAN MARUBUCIYAR Duk karyar kada Yar mahaukaciya Neman na kaina Bani da zabi Bak'a ce Kutkale Makauniya ce Mage Duk nisan jifa Idan ka raina inda kake Dutse Alkalamin kadarata Bani da zabi Dakika Biyar Now *Da CIWO A ZUCIYATA* *Tallah, tallah, tallah* *SECRET DE LA FEMME DU MANGA* _Gidan Kamshi, Sirrin Manyan Mata, nesa tazo kusa,Amarya ,Uwar gida,Ango da mai gida Har ma da yan mata da samari shin kuna sane da cewa HAJIYA FUSAM ta shirya tsaf domin gwangwaje ku da turarakunta masu dankaran kamshi? Tare Kayan gyaram jiki na musamman ,wanda daga nesa kamshin ki kadai ya wadatar ya isar da sakon zuwanki waje,gidan ki kuwa sai ya zam abun kwatance wajen kamshi, kar na cika ku da surutu bara in fara zayyano su_ Farar Humura Bakar Humura Humura special, humura de bain Humura epicé Lait de nuit Parfums désodorisant Parfums rideau et dras Lait de nuit Alkam Kulakcam *Waɗannan kadan ne daga bangaren turaran ruwa* Gagab, sandal flex, Durot, durus, sandal fleur, tafarce, farce, sandal bangui, sandal, hypotonic sandal, al'ut, coktail creation VIP, Gajiji, Mankaji, turaran wutar labule da cafet, Aba malan, boulettes *Munada bangaren gyaran jiki kamar haka:* mai mai saka santsin jiki, mai mai kanshi, Kayan gyaran jiki mai saka fata ta yi santsi da laushi, kayan gyaran jiki mai saka fata ta yi fari, Sabulu mai saka fata ta yi haske, sabulu mai saka fata ta yi santsi, sabulu mai goge yanayin fata, mai wanda baya saka fari mai gyara fata Sayen na gari mai da kudi gida,sai an gwada akan san na kwarai💃💃 Hajiya Fusam na zaune a kasar Niger domin yin magana da ita kai tsaye tuntuɓi wannan number 97 82 44 94 *SECRET DE LA FEMME DU MANGA* Gidan Kamshi, Sirrin Manyan Mata💃💃💃💃💃 Sunna cikin tashin hankalin wannan su su kadai a gida wani ya same su, domin tana cikin dakinta tana jan carbi wani yaro ya shigo yace ana salama da ita , da ta tambayi waye sai cewa ya yi wani ne wannan dake zuwa koda yaushe wajenta ne Har ga Allah har gagawa take yi wajen mikewa daga saman salayarta ta cenza hijab da dan sauri ta leka ta sanarwa Mama sannan ta fito duda hasken gari ta fito hankali kwonce ta shiga duduba shi Ai kam shi din ne, da farar jalabiya a jikinsa yana tsaye hannu daya goye a bayansa daya a cikin aljihunsa yana ta faman kada kai kamar wanda ransa ke bace Da sasarfa ta gaishe shi bayan ta dan duka, sannan ta mike tsayinta tana kokarin yi masa bismillah kamar yadda suka saba idan ya zo wata mahaukaciyar mota ta nufo ta parker daf da tas har kamar zata gogi tasa Irin tashin hankalin da ta ga ya shiga sai da cikinta ya so murdawa, a hankali ta mayar da hannunta da ta fitar dan yi masa bismillah zuwa cikin gidansu Mata biyu ne suka fito, kamar yaya da kanwa haka Wace ke taunar cingan din ce ta bude cikin motarsa daga gaba ta dauko wayarsa tana ci gaba da tauna cingan din ta danna wayar hannunta ta shiga amsawa kamar haka" Gamu gashi bobo, yanzu fada min yaya zan yi in kashe localisation din" Daga dayan bangaren akai mata bayanin yadda zata kashe ainahin abinda ya basu damar gane inda ya zo daga fitowarsa daga gida bayan ta saka shi a kason kwana uku kennan Tana kashewa ta juya wajen motar tasa ta maka wayar da jikin madubin motar, ji kake tartsatsa karar fashewar madubin motar kafin ta karaso inda yake tsaye mundil a gabanta jikinsa sai rawa yake sai wurna wurnatu yake kai kace in ya sha iska ya dauketa yana iya makata da kasa, domin ita dinma a ginne take koda bata kai Khausar din ba to fa ta kusa kaita ne dan ko a yannayinta ba siririyar mace bace Kare masa kalo take yi tana taunar cingan din nan yana wani kas kas kas sannan ta juyo bangaren Khausar wace ke tsaye, ama kana ganninta ka ga wace ke shirye ta iya aukawa da gudu in ya kama dan kuwa abinda ya dakatar da ita ta yiwu maganar da yake yawan fada mata ne cewa shi din tsayayen namiji ne a gidansa da waje! "Elhaji Mujaheed kennan, wai tsakaninka da Allah a tunaninka shikenan har ka sha bulus ? Kai yanzu a cikin kwakwaluwarka tunaninka nima irin sauran biyun cen ne da ka hade gida daya kake wulakantawa? Ai ina tunanin tun a lokacin da na ki ka hadeni gida daya da matanka ya dace ka san ni ba irinsu bace, ko nace tunda ka san me ka aura ya dace ka taka a hankali, kai yanzu har wani sankon dan daba ne a haka? Kai har dan jagaliya ne? Shine ka tarda babanmu kasuwa yana cinikin hatsinsa ka tayar masa da hankali a cikin jama'a kana masa ikirarin a min magana aure kace zaka yi ba ruwana a cikin maganar kuma gida daya zaka hadani da matar in ba haka ba daular da ake mora sanadinka tsaf tana iya tashi daga sunnanmu? To kai ai baka san da tsohuwar yar iska kake zaune ba sai yanzu, gidan nan da ka bada baka ga sai da aka baka nono ka sha ka kuka damuki abinda ka damuka ba kafin ka yi kyautarsa? Ai kyautar gida da ka yi tun kafin ka aure ni ne , a duniya muka watse ka bada kyauta dan ka yaba kuma sai da saurayina ya tabatar da sunnan gida sunnana ke sama kafin na yarda da kyauta ta zama tawa, kai yanzu kana tunanin dan kana da yan kudaden nan ka fini mutane ne ko wani haukan ke kada maka cewa kana iya kwace gida? Da nake ce maka daga ni ka rufe ka dauki maganar a tatsuniya kennan shine ka nufo wannan zaka kawo min mu jera??????" Ta fadi wannan din tana nuno Khausar wace idannuwanta suka yi waje tsabar tsoro da firgicin abinda yake faruwa, haka kuma kafin kace meye wannan an fara tsalakowa kallonsu, kuma an rasa mai cewa ufan domin fadan kamar mai digi ne da dadin kallo a lokacin har sai da matar nan ta nufota a tsayen da take bata ankara ba ta kama hijabinta ta aniya neman kwashe shi daga jikinta Nan fa hankalinta ya idasa tashi, jikinta haka yake rawa tana rikewa matar na ja Da karfi makociyarsu ta karaso ta aniya shiga tsakani haka yayar matar itama ta shiga Karshe dai da kyar makota uku suka hanna wannan lamari da tuni ya rikita hankalin Khausar ya kuma so ya zauta tunaninta, Tunda take, tunda ta malaki hankalin kanta a anguwar nan bata fito ba fan kwali ba, sai gashi a yai za'a cire mata hijabinta daya da ya fi sutura a jikinta domin a kasan ba wani abin a zo a gani bane dan kuwa zani ne kawai saman yar ficiciyar riga ta shan iska "Au, fadan area zaku mayar da shi ko ku din danginta ne?" Matar ta fada da tarin rashin kunya tana harar makociyar Mama Makociyar Mama da suke abin arziki sosai ta tareta tana fadin" Eh mu iyayenta ne, da komaima, babu abinda zai saka ki cire mata hijab a banza a wofi, mema ta maki ne yarinyar da ba komai take cewa ba? Shekarunta nawa a anguwar nan bata taba yi da kowa ba, haka a makaranta da tana yi da koda sau daya ne an sani, to koma menene ba zaki ci mata zarafi a gaban kartin maza ba, ku kuwa su Isuhu kunna tsaitsaye me kuke jira ku gama gani kafin ku tsawatar ku hanna a zo har anguwa a wulakanta yar gidan mamuda? Ai kam ba adalci a lamarinku dan na tabata da shine walahi sai inda karfinsa ya kare!" Sai da ta yi wannan maganar ne kuma samarin suka shiga hargowar rabiyar fadan da yannayi irin na dabacin nan sunna nuna ko ta bari ko su far mata, tuni aka samu aka sake matsa Khausar hanyar gida, da lalube ta juya tana son bude gidan ta shige ta ga mahaifiyarta ta ja kofar ta fito domin ta kasa hakuri zuciyarta sai harbawa take cike da tsoron menene wannan din kuma Da wani yannayi na yan daba matar nan ta karewa makociyar mama kallo a lokacin da Mamanma ta fito ta ce" Mama, kina jina? Zamu tafi, ama ba hakan na nufin zan kyale yarki bane innhar bata fita daga harkar wancen mutumen ba, da kika ganshi a cen mijina ne, a yanzu dai a gidansa nice ta uku, a cikinmu duka haka kirarmu take dan yana sin manyan mata, Mama nima mun hadu a yawon ta zubar da shi ne ya aureni , ya bamu gida ya bani mota, wannan fa zan iya ce maki zaku samu , sai dai in zaku iya jure hali irin nasa da kuma nawa, dan na rantse maki har saman gadonta yana iya kawo mace ya warwareta sala sala bale idan ya rainata, wulakanci kala kala da gori zata ringa gani a rayuwa dan baya auren yayan masu kudi sai ya nemi yayan talakawa ya wankesu tsaf ya amshi yar ko me ta je ta fada a gida sai dai a bata hakuri a dawo da ita, ga kuma nawa a gefe, dan da kika ganni a nan mama abin kunya ne a cikin kawaye ace wancen ba wada haushin ya karro min wata, babu abinda na rasa shima ya sani, in bama masifa ba shi fa halitar da zai gamsar da matan irinmuma bashi da ita ama haka yake aurowa ya halaka a gida, ai na fada maka ni da kai shege ka fasa Walahi sau dubu zaka hau mace sai na samu jikeken Kato mai sunna kato na kawar da ƙishirwa haka kuma mun riga mun zamewa junna karfen kafa dan ba kari ko uban wa ya yi maka tsaye nice nan na fada, in kuma kun yi gardama ku aura masa ita , ke ki yarda ki aure shi ki zo ki sameni ina nan ina jiranki dan sai na........."......................... ........ Kalaman da kunnayenta suka iya ji kennan ta samu ta karasa dakin Aba da gudu ta zube nan saman kujera ta rufe kanta da hijabinta tana rizgar kuka tamkar kanta zai rabe biyu Wasa wasa Mama ta dauki minti talatin kafin take shigowa, ko tace take shigowa tare da Aba, wanda idannuwansa suka gama kadewa suka yi jajajir har hada hanya yake yi wajen karasawa inda Khausar din ke kwonce Murya a tausashe bayan ya zauna ya ce" Kuka kike yi tun dazu? So kike yi ki hadawa kanki ciwo ne? Tashi mana autana, ya isa hakanan" Tunda ta ji muryarsa a farko kukan ya tsaya , tana jin me ya fada ta fashe da wani kukan mai karfin gaske ta dago fuskarta da ta yi jajajir gashin idonta ya hade ya yi wani irin luhu luhu da shi ta zubawa Baba idon tana girgiza kai a raunane ta sake mayar da kanta ta dukunkune a cikin hijabinta cike da jin kunyar baban da kuma tarin kunyar kalaman da matar nan ta ringa fada a gaban su Mama wa'inda ita dai a kankin kanta tunda Allah ya haliceta babu inda ta tsaya ta ji kalamai mararsa da'a irin wadinnan, sam bata tare da mutane masu gurguwar yare, haka a anguwa bata shige shigen yaren mata masu sakin harshe sunna maganar mazajensu a bayane ba dan raha ba, shi yasa abin ya wani irin daketa ta kasa kallon kowa a dakin Auta ne ya karasa ya zauna yana kama hijabin nata ya ce" Aunty, kin ga kuwa yadda aka musu? Aba fa ya je har gidan da ni yace to kar ya kuma gannin kafar kowa a gidanmu, in fada maki harda shi uncle din Aba yace ya rabaku kar ya kuma ji, kuma sai ki ringa yin kuka? Tunda Mama ta yi kiran Aba muka fito daga kasuwa muka zo fa" A birkice ta dago, ta dubi Aba, har lebenta na rawa rawa ta ce" Aba, kar ya kuma zuwa? To wa zai aureni in bai zo ba Aba?" Mama dake share hawaye a kofar dakin ta shigo kamar an sanyota ta zubawa Khausar ido Muryarta a raunane ta ce" Ke? Kina da hankali kuwa?, Ko tunanin kin gaza samun mijin ya fara taba kwakwaluwarki ne? Kina nufin in akace ya zo ya aureki zaki iya yarda bayan duka kaf abinda kika gani kika kuma ji? Yau ba dan Allah ya sa ana mutunci da makota ba ai da sai sun gama wulakantaki tsaf sai dai ki mutu in mutuwa zaki yi dan kuwa da y'ar bariki ta hado ki fa Khausar!, Ke wai shekarunkima nawa ne? Ko hamsin ne da ke sai aka yi me? Ko mun mutu mun barki ke daya a gidan nan sai aka yi me? A kanmu farau ne? Ke ba yar bariki bace, ke ba mai wulakanta mazan bace, kadararki ce fa ta zo a haka kuma shikenan sai ki dauki ciwo mai tsanani ki sakawa zuciyarki? Khausar ina sane da halin da kike ciki na ki baki dama ne kar abin ya zama shirme ki kasa rike kanki a cikin gida, ama tunda haka ne ya isa haka, ya isa hakanan khausar, miji idan ya samu to in bai samu ba babu yadda zamu yi, abinda na sani daya ne tak shine idan kika wulakanta kanki ta hanyar bin maza kin cucemu kuma kin cuci kanki, ki ci gaba da kula da mutuncin kanki da namu har yadda Allah ya yi!" Daga haka Maman ta yi gaba ta barsu da binta da Kallo, Baba ne ya tausasa muryarsa ya yi mata nasiha sosai , kafin shima ya tashi ya fice masalaci Da raunin zuciya da komai ta karasa wajen salaya ta samu ta yi sallah sannan ta kwonta a nan har dare ya fara yi Kiran da wayarta ke yi ya sakata laluba ido har yana rufe mata dan abinda ke ranta ta daga bayan ta ga sunnan mai kiran ta yi masa salama a sanyayen da yannayinta yake Kasancewarsa mutun daya kwalin kwal dake saurin cenkar yannayinta, hakan ce ta kasance yanzunma, harma kamar ya mike ya fice daga cikin mutane ne ko menene muryarsa a tausashe ya ce" Me yake damunki? Dazu ance baki je aiki ba baki da lafiya, wht hpn?" Ya karashe hapn din yana gagawar dakatar da nurse din da ta shigo da nufin yin magana kan list din wani magani da aka rubuta za'a ba wani patient a asibitin, domin du a rikice suke tunda ya masu dirar ba zata sai guje guje suke dan kar ya kama su da wani laifin domin ya samu abinda ba daidai ba yana cikin fadan ne ya ce da su ohk tunda haka ne da shi suke maganar, kuma sun san me hakan ke nufi shine fa du suka rikice yana office din docter Ibrahim sunna maganar abinda yake faruwa a asibitin ne ya danna mata kira Rabewa Nurse din ta yi kanta a kasa , shi kuwa ya saurara yana son jin amsa daga Khausar A hankali ya furta" Khausar? Ko kin yi barci ne?" Khausar ta lumshe idannuwanta, a hankali wasu zafafan hawaye suka shiga bin gurbin idannuwanta, muryarta a shake ta ce" Aa, ban yi ba" "Kuka kike yi ne? " Ya fada a sanyayen da ya saka nurse din nan da mahaukacin mamaki satar kallonsa, domin tunda take bata taba jin dai ya yi doguwar fira da su ba in ba shafar aiki ya yi ba, ama kuma in ya kamaka da laifi a kan marar lafiya yadda ka san zai cinyeka danye haka yake damkarka, a ranta ta ayana' ta yiwu da Hajia yake' watau Mama, dan kuwa du duniya ita kadai ce suka san ko asibitin ta zo idan zai mata magana to fa a sanyaye muryarsa take, dan kuwa hajia kakarsa su caku be tace ba'a yi yace sai an yi, matarsa kuwa basu taba ganninta ba, basu san yaya mu'amalarsu take ba "Rashin lafiyar ne yau ake yiwa kuka? Yayama aka yi baki da lafiya ama baki sanar min ba? Kin sha magani ne????" Ya sake fada a hankali sosai a kuma sanyaye sai dai kuma abin auna zafin zazabin jikin marar lafiya dake hannunsa ya masa riko mai karfin dake nunin da shiru shirun da yake yi ta yiwu wani abin ya hanna shi fido ainahin abinda ke ransa a irin wannan lokacin " TAUFEEK, Mujaheed ne....." Sai kawai ta saki kukanta a raunane har tana dan dafe gaban kirjinta dake mata zafi.....dan sai ta ji inma bata fadawa TAUFEEK ba ai an gama cutarta, dole ya san damuwarta dan bata da amini abokin sirri sama da shi A hankali ya lumshe idannuwansa da suke karra girmama bacin ransa, a saman lebensa ya maimaita sunnan yana hangen Mujaheed din a idannuwansa Khausar ta dora da fadi " Babu irin abinda bai ce ba a tarayata da shi, har cewa ya yi idan ya aureni ba ni ba kai, haka na so masa biyaya dan aure akace darajar aure na gaba da komai kuma mijina zai zama wanda aljanata zata kasance karkashin kafafuwansa, TAUFEEK babu abinda ban gani ba na tijara a tarena da shi ama na sakawa raina zafin kishi ne idan dai na shiga gidansa ai shikenan, ashe ashe wani abin ke jirana a zamana da shi??????, Taufeek ya min aalkawarin karshen watan nan zai turo, dama shiru maganar bata motsa ba ashe ashe da abinda ke tare da shi? Yau matarsa tamkar zata zane ni, har hijabina ta kama zata cire min a kofar gida, ta zazageni tass a gaban su Mama da kyar aka rabani da ita, TAUFEEK ni na ga tashin hankali karshe dai yanzu baba ya min tsakani da shi wai kar ya kuma zuwa, kuma yanzun ko ya zan samo wani????" Magangannunta babu wanda bai narka masa zuciya ba, a tarin tashin hankalin da take ji zai iya cewa a yanzu da take fada nasa babu wanda baya ji Hankalinsa ne ya nemi tashi sosai What????? Shine abinda zuciyarsa ke maimaita masa a matsayin tambaya Mikewa ya yi daga zaunen ya nufi ficewa a office din dan sai ya ji ya masa kadan dan bacin rai Sai da yya fito filin Allah ya iya budar bakinsa ya ce" Matarsa? Ta cire maki hijabin ne?" ......a tarin tambayoyin dake harshensa bai san dalilin da yasa wannan ta fi tsaye masa a ransa ba, ko dan ya san khausar da kafa kafa da mutuncin kai ne? Ya kuma san anguwarsu yadda ta tara tarin maza kala kala ne? Sai kawai ya ji ya fi son jin bayanin nan fiye da kowane A hankali ta fitar da huci mai zafi ta ce" Sun dai dan ja ama su Maman Abdul Rahman suka rike, kai dai kokowa kamar tashin duniya sai da su isuhu suka kama fa...." "Suka kama me?"ya fada a dan hanzarce har yana dan saka hannunsa cikin aljihun farar rigar dake jikinsa ya dan jimke hannun nasa yana sauraronta Khausar ta ja numfashi ta ce" suka kakama tasa da kawarta suka hanata dukana...." A hankali ya bude idannuwansa dake dan lumshe kasa kasa ya ce" uhum, shine kike kuka ? Khausar tsoro gareki ko? " "Ni ba kukan dukan nawa bama nake yi, yanzun kukan kuma yaya zan yi naa samo wanin nake yi ai TAUFEEK " ta fada a sanyaye tana rafka tagumi hadi da zubawa kofar dakinta ido Ya dan dauki lokaci bai yi magana, daga bisani ya ce" Khausar duka dukanki shekarunki nawa ne da zaki takurawa kanki haka? Kin cika saka damuwa a lamarinki Khausar bayan kin san komai lokaci ne ko?" "A hausa? A shekaruna, a yannayin jikina kaima ka san ai na tsufa ban amsa kiran mai aure ba, duka duka tserayata da kai nawa ne? Kaima ka yi auren nan fa kai namiji bale ni?, Dole na damu Taufeek "" " Ban ki ki damu ba, ko ba komai shekarunki da kike ikirari sun kai ki damun, ama kar ki manta Allah keda komai, ke kamar wace ta haife duniya in kika tashi zanen namijinmaa da kike so sai ki ce mai mace biyu ko uku haka, mai ya'ya ke ga wace ta gama zama uwar duniya ko?" Ya fada a dan kausashen da ya sakata jin kamar zata saki murmushi du kuwa da halin da take ciki A hankali ya ci gaba da fadin" ki ci gaba da yin abunda zai fisheki, ki kwontar da hankalinki, idan kika gama wannan aikin daga cen zasu baki takardar asibitin da zata dauke ki, ba zama zaki yi ba aikinki zaki ci gaba da yi domin ko hutun kwana daya ba za'a baki ba......, Ki sani kowani bawa da irin kadarar rayuwarsa, Mujaheed bai kai ya sakaki kuka ba besty......" A hankali ta ce" ka ce idan na gama za'a bani takardar daukan aiki? Kana nufin daga nan zan samu aiki?????" Tabatar mata ya yi ba tare da ya ja maganar ba Da sauri ta mike tana fadin" TAUFEEK kar ka min wasa mana, aiki fa kace? Aiki aiki dai? ....." Amon muryarta na nuni da zumudin dake cikin zuciyarta, hakan ya sa ya dan rage bada tabacin dake harshensa ya ce" komai ai na Allah ne, akoy kyakyawar fahimta tsakaninsu da Aba, kuma tunda ya sama maki stage din nan yace min kina gamawa za'a kaiki asibitin da taa daukeki, ko nan din ko wani wajen" "Wayo allahna, INNALAHA MA'ASABEREEN...." Ta furta a sanyaye tana sauke zazafan murmushi mai gauraye da tarin farin ciki A hankali ta ce" Hakan na nufin, zan samu aikin yi nima, na zo ina taimakawa su Mama ko????????" 💔💔💔💔❤‍🩹❤‍🩹💔💔💔💔 *DA CIWO A ZUCIYATA* 💔💔💔💔❤‍🩹❤‍🩹💔💔💔💔 _MALLAKIN_ *SAJIDA NIJAR* *FREE BOOK NE* 2️⃣6️⃣ LITATAFAN MARUBUCIYAR Duk karyar kada Yar mahaukaciya Neman na kaina Bani da zabi Bak'a ce Kutkale Makauniya ce Mage Duk nisan jifa Idan ka raina inda kake Dutse Alkalamin kadarata Bani da zabi Dakika Biyar Now *Da CIWO A ZUCIYATA* *Tallah, tallah, tallah* *SECRET DE LA FEMME DU MANGA* _Gidan Kamshi, Sirrin Manyan Mata, nesa tazo kusa,Amarya ,Uwar gida,Ango da mai gida Har ma da yan mata da samari shin kuna sane da cewa HAJIYA FUSAM ta shirya tsaf domin gwangwaje ku da turarakunta masu dankaran kamshi? Tare Kayan gyaram jiki na musamman ,wanda daga nesa kamshin ki kadai ya wadatar ya isar da sakon zuwanki waje,gidan ki kuwa sai ya zam abun kwatance wajen kamshi, kar na cika ku da surutu bara in fara zayyano su_ Farar Humura Bakar Humura Humura special, humura de bain Humura epicé Lait de nuit Parfums désodorisant Parfums rideau et dras Lait de nuit Alkam Kulakcam *Waɗannan kadan ne daga bangaren turaran ruwa* Gagab, sandal flex, Durot, durus, sandal fleur, tafarce, farce, sandal bangui, sandal, hypotonic sandal, al'ut, coktail creation VIP, Gajiji, Mankaji, turaran wutar labule da cafet, Aba malan, boulettes *Munada bangaren gyaran jiki kamar haka:* mai mai saka santsin jiki, mai mai kanshi, Kayan gyaran jiki mai saka fata ta yi santsi da laushi, kayan gyaran jiki mai saka fata ta yi fari, Sabulu mai saka fata ta yi haske, sabulu mai saka fata ta yi santsi, sabulu mai goge yanayin fata, mai wanda baya saka fari mai gyara fata Sayen na gari mai da kudi gida,sai an gwada akan san na kwarai💃💃 Hajiya Fusam na zaune a kasar Niger domin yin magana da ita kai tsaye tuntuɓi wannan number 97 82 44 94 *SECRET DE LA FEMME DU MANGA* Gidan Kamshi, Sirrin Manyan Mata💃💃💃💃💃 Wannan karron bai bata amsa ba ta ci gaba da fadin" TAUFEEK, ban san harshen da zan yi anfani da shi dan yi maka godiya ba, TAUFEEK haduwata da kai alkhairi nake ta gani a koda yaushe, ina jinka a raina tamkar dan uwana na jinni, sanadiyarka nna hadu da haske kala kala, TAUFEEK duba ka gani yadda Hajia ta daukeni, yadda Mama ta daukeni, uwa uba gashi yanzu Aba ya sama min aiki, ka ga ko nawa nake samu a wata fa hakan na nufin zan iya kawo baban talafi wa ahalina harma nima na yi kyauta na yi sadaka ko? Irin nima ma'aikaciyar nan har na siyo kaji birjik a yi washa washa a gidan nan ko..?????" "Khausar" ya fada a cen kasan makoshinsa Khausar ta dakata daga share hawayen ta amsa itama a cen kasan makoshin nata TAUFEEK ya yi dan murmushi ya ce" ki daina kukan mana, baki san bana so ba?" Khausar ta saki murmushi hadi da sakin hawayenta ya gangaro ta ce" To, na daina TAUFEEK....." Ya yi murmushi ya ce" Bana so na ji wani kukan a kan wancen kin ji?, Sannan a koma aiki gobe bana son wasa da aiki fa" Khausar ta yi yar dariya tana fadin" in ji wanda baya tsayawa ya yi jarabawa, TAUFEEK jira nake a koma makaranta zaka sha matsi dan ba zan taba barinkaa ka sarara ba sai ka ciyo min takardar nan in sha Allah " Shima murmushin ya yi yana jin dan sanyi a ransa jin zata dawo normal, watau besty dinsa mai rigimarsa wace shi kadai ne bata tsoro ama sauran al'uma du tsoronsu take Da wannan suka yi salama, itama har ta je ta samu iyayenta ta sanar masu wani abun farin cikin, wanda ya dan sanyaya zukatansu baki dayansu Washe gari da sasafe ta yi tafiyarta wajen aikinta, anguwarsu kuwa a ranar wuni aka yi ana shafa wannan labari, guri guri har bayan layinsu sai da zancen ya kai , yawancin mutane fadi suke madallah dama da ta ki aure ai ba wani abu bane dogon buri ne ita likita sai mai kudi zata aura, wasun su ce yawace yawacenta da ya yi yawa ai dama da wahala ta auru, wasu suce sa dai ga karyar boki ita yar boko uba da uwa sun daure mata, daidaiku ke jimamin lamarin da fatan Allah shi kyauta domin irin anguwar nan ce da daidaya ne suka tsira da boko su dinma maza ne, ita din ce kawai ta yi dogon karatu irin na asibiti da bashi da lokaci har ta kai warhaka, a yanzunma da take aiki irin na gadi wanda take kwana a cen an sha ceece kuce, mahaifinta ne kawai mutun mai ra'ayin kansa, ya kuma yarda da yarsa, da ba wannan ba da tunima an saka ya cireta a harkar karatun Sannu a hankali Khausar ta gama watani ukunta da ta dauka a babar asibiti bangaren emrgency A wadinnan watanin uku da ta yi tun daga kan mai gadin kofar asibitin har zuwa manyan ma'aikatan babu wanda zai ce ga abinda ta masa marar dadi ko na raini ko aka kamata da wasa da aikinta ko kula samari ko dai wasu halayan mararsa dadi, ko gadi Khausar take yi ba zaka ga saurayi ya zo wajenta ba, haka kuma manyan doctors dake aiki maza wa'inda suke da dabi'un kula mata babu wanda ya matsewa Khausar waje dan sun san da sunnan wanda ta shigo wajen, watau ubansu ne idan suka yi wasa komai na iya faruwa, mutumen da yake abin wasa a wajenta su dodonsu ne A ranar da ta gama harda dan hawayenta , a lokacin ne aka tabatar mata kwana daya tak take da shi na lahadi ba zata je aiki ba, likiti ta tabatar ta tafi tunda sasafe babar asibiti mai sunna *LAFIYA* wace aka ce nan ne zata je ta yi aiki a matsayin ma'aikaciya A ranar farin ciki a gidansu ba'a magana, ta nemi layin TAUFEEK har ta gaji da nema bata same shi ba, ta so tafiya gidan a washe gari sai dai kitso da wankin kafar da ta je da kuma wajen Fusam dan amsar wasu yan kayayakin gyara a dole ta yi dare bata biya gidan ba, ama ta ci gaba da neman layinsa cike da mamakin rashin samunsa , sai da dare ya yi ta hakura dan yanzun in dai ba shi ya yi kiranta da dare ba to fa bata kiransa dan har yanzu bata gane manufar matarsa a kanta ba Shi kuwa a irin lokacin da take nemansa wayarsa sam baima san inda take ba, aikin da ya gagabo masu shi da manyan ma'aikata suke kai, watau tantancewa da fitar da kwararu masu son aikinsu da kyma ware maus shiririta ciki harda asibitinsa clinik dinsa privet mai sunna *LAFIYA!* wace a gobe litinin yake da niyar shigarta da karfinsa dan ba zai taba lamunce abubuwan nan ba, manya manyan abubuwan dake hargitsa shi a aikinsa shine likitan da bai iya aiki ba, yana iya yin komai a kan haka, shi yasa yake da taka tsantsan da tsauri, dan a ganninsa du ma'aikacin jinya ko na dabobi ne ya dace ace kwarare ne a fannin aikinsa ba haure ba, dogon aikin da ya saka shi bada kamar shekara da shekaru kennan kuma bai ga alamun zai daina yanzu yanzu ba Tun karfe bakwai Khausar ta gama shiri mai sunna shiri, shirin da Mama ke binta da kallo cike da mamakinta da kuma addu'a a kasam zuciyarta, domin bata taba gannin yarinyar ta yi shiri haka ba, Ba wai makup ta makawa fuska ba, ama ta saka kwali daidai misali ta kuma saka dan jan baki mai ruwan kasa dan daidai da lebenta na kasa Girarta cajeta ta yi sosai, kitson da kai mata kuwa sai ta daura ribom mai kyau ta daura dan kwalin atampar da ta saka doguwar riga wace Mama ta dinka mata sannan ta dora hijab mai ruwan sararin samaniya mai yar walwali a jikinsa sai jaka ruwan hijab din da takalmi plate ruwan hijab din sai dan mayafi da ta yafa wanda yake shara shara ne du girmansa dan ba abinda ya rufe a tsarin halitar jikinta wace zuwa yanzu tumbin nan gana dayansa ya sasabe ya mugin zube sakamakon wahalhalun da ya shiga da kuma dan hadin da take masa na bawan albasa da lemun tsami da cita tana sha wanda sosai ya sake sabe tumbin ama bayan tumbin babu abinda ya ragu kama daga duwawunta da cinyoyinta, sai gayu da ta fara koya na mamaki a wajen uwar gidanta docter Rauda da kuma hajiyarta Fusam, ga wani tsararen kanshi da take fitarwa mai sanyi ba mai hayaniya ba Tsuru ta yiwa Mama cike da jin kamar a takure take ta juya tana fadin" Mama bari dai in dauko hijab, ga jakata da rigar aikina a ciki Mama" Mama da dan sauri ta ce" Ke Khausar zo, me wannan din ya yi?" Sai kuma ta yi shiru tana dauke kanta a ranta tana mamakin yau itace da cema khausar kar ta fita ba hijab???? Tana shirin ce mata ta dauko hijab din Aba ya shigo yana fadin" Ina Khausar din maza zo ga dan sahunki nan, shi zai ringa kaiki yana dauko ki, ki tabata wayarki da caji ga wannan katin ki loda dan kiransa in kina so ya dauko ki, ga kuma kudin abinci, a kula sosai yar albarka a kula bana son biye biye, bana son ka je aiki ka ringa abinda ba shi ya kaika ba kin ji? Ki kama mutuncin kanki kin ji ko?" Ya idasa fada yana riko jakarta dake gefen mamanta ya Sakkata gaba suka fita Mama ta yi murmushi bayan ta rakata da addu'a ta mike ta shiga fitar da kayan abincin da aka kawo tana dubawa, harda su kwai da doya da su waken suya da madara, tunda ta kawo albashinta harda su kuka da mahaifinta ya raba biyu ya bata rabi wai ita bata son ko sisi, da kyar shima uban ya amshi duka, ama gaba daya kudin a hidinar gidan ya zuba su, ya siyo matta wata waya yar madaidaiciya da hijabai sababi har biyar, ya masu siyaya suma sannan ya daukar nata dan adaidaita sahu ya kuma ware kudin abincinta.....lalle a wata ukun nan sun mori albashinta sosai, ama na watan nan sun fi morarsa domin na watanin da suka shige a hidinar kannenta ta saka kudin kafff Tunda aka ajiyeta a bakin makeken get din asibitin ya ringa taslima a zuciyarta, lalle a yadda ake kwatanta masu asibitin nan ba'a fadin ainahin yadda yake Tafe take tana tambayar baban wajen reception har ta karasa tana karra bin komai da kallo tamkar wace ta fita daga kasar ta je kasar turai Madubai ne, shukoki ne, ma'aikata ne sunna ta aiki sai sake gogewa ake yi bayan ba wani dati da wajen ya yi , haka kuma komai a tsare ga kanshi dake tashi ta ko'ina Ajiyar zuciya ta sauke cike da samun kanta a rudu, yanzu a nan ne zata yi aiki? Ma'aikatar da akace gagaruman likitoci ke cikinta, du wani likita mai ji da kansa kana samunsa a nan cikin sauki, to ita a matsayin yar goge goge ta zo nan ko Da ido take bin masu aikin, sai ta samu kanta da jin sanyi sanyi da ta saka sabuwar atampar nan, yau da ta rasa wajen buya da bata dan kimtsa kanta ba Wata mata mai riga ruwan goro ce ta kula da yadda Khausar ke bin mutane da kallo ta dasu a waje daya tunda ta shigo baban filin dake rarabe da mutane daban daban kowane a bangaren da yake nasa aiki ta tunkarota tana tambayarta ko ta bata ne? Da dan barin baki Khausar ta mika mata ambulop din da aka bata tana binta da kallo, ita kanta mai wanke dakin masu haihuwar nan sai ta dauketa aiki jama'a, kwas kwas da ita harda farin gilas na yan gayu Dubawa ta yi sai ta kalleta da sauri ta ce" Kai, to zo maza na raka ki sunna sama yau oga na tantancewa bakinma du sunna sama maza ciro rigarki saka mu je wajen chef sai ya saka ki bangaren da kike, Allah dai ya sa ki samu karbuwa dan baki taki Sa'a ba gaskiya a hasale oga yake kuma yau yake fara tantancewa , Allah ya da kin iya aiki yar nan, dan kuwa daya bayan daya sai kun saka ruwa ne da sauransu aikinku dai na likitoci....." Cikin Khausar sai da ya amsa, nan take ta ji wani shaka da tsoro na neman aurar zuciyarta Tantancewa, dama a makaranta ana cewa itafa asibitin nan ba'a wata ba'a yi tantancewar nan ba, tsaf ake iya cireka a maye gurbinka da wani ba wasa, shi yasa likitocin kowa ke aikinsa ba ji ba gani domin ko dan albashin wajen ba zaka yi sake a yi maka sakiyar da ba ruwa ba Biye take da ita har suka karasa wani tankamemen hl wanda sunna shiga kanshin wajen da sanyin wajen ya sake sakata a hali na tsoro da tunanin lalle yau zata samu baban abu da ake kira ta leko ta koma, dan bata idasa fita a hayacinta ta ringa kallon mutane tamkar ba yan adam ba da irin tarin kayan aikin wajen sai da suka karasa aka amshi ambulop dinta aka duba aka yi mata tambayar ina kit dinta na kayan aiki irin su abin auna zuciya abin daukan zafin jiki dai da sauransu ta nuna shi hannunta na dan rawa aka umarceta kan ta fitar da su ta je ta layu wani bangare gefen hagu inda wasu bayin Allah ke laye kamar an masu mutuwa kowane na nazari da addu'a a zuciyarsa domin su kusan bakwai ne kuma dukansu baki ne yau suka fara zuwa asibitin A kala sun dauki minti sama da arba'in ana ta karra gyare gyaren wajen Ba wasa a lamarin Kowa kai kawo yake cikin manyan har ta ga an dana wata katuwar tv ta nuna shigowar wasu motoci uku balbalin asibitin sannan aka kashe tv din aka sake tsatsaresu da duba kamar wa'inda suka aikata katon laifi duba irin na to fa ga maza bisa kanku, ya zamto harta manyan likitocin sun shiga taitayinsu sunna sake bin dukkan abinda suka san na iya zame masu matsala sunna tabatar da sun daidaita komai da komai Minti kusan sha biyar kofar mai dauke da madubi ta wangale, Shine a gaba, yana sanye da bakin wando dogo na sweet, sai farar riga kal a ciki sai cravate mai ruwan maroon da dan fari fari jikinta, sai rigar likitoci fara kal wace ta dan sauka har kusan gwuiwarsa kadan, sai abin awon bugun zuciya dake rataye a wuyansa, hannunsa na hagu daure da agogo kirar kampanin ROLEX na daman kuwa ya dan tatare rigar har zuwa kaurin hannun nasa wanda ya bayanar da jijiyoyin hannun rado rado da tarin kwarjini da fuzga irin ta cikaken gamsheken namiji ta tafi da tafia har ya karasa kusa da baban teburin kwalbar da chef ke biye da shi da sauran likitoci biyar mata biyu maza uku manya manyan likitocin da ake ji da su a kasan nasara biyu sai hausawa uku kowane cikin shiga tasa shima irin ta likitoci ya karasa nan suka dan zanta kasa kasa inda baka jin komai sai dan abin AC dake watsa sanyi domin ko numfashinsu ba fita yake yi da karfi ba A hankali ya ajiye farar takardar da aka bashi mai dauke da bangare bangare na du wani ma'aikacinsa na asibitin nan harda baki ba tare da ya karanta ba ya mike tsayinsa a gabansu ya dauko dubansa tun daga cen kurua kurya ya ringa binsu da kallo a hankali har ya dawo bangaren da ake nufin nan ne bakin suke su su takwas cif kennan Lokaci daya Gabanta da nasa suka buga, Bugawa mai tsananin gaske A hankali ya lumshe idannuwansa ya kai hannunsa na hagu ya dan sosa gefen hancinsa sannan ya sake daure fuskarsa tamau tamkar bai taba sannin wani wai shi daria ba a lokacin da ta kai hannunta na dama ta murza idannuwanta ta sake murzawa ta bude su tarrr a saman fuskarsa da matsanancin mamaki ta budi bakinta tana dan kokarin mikewa duda rawar da jikinta ya karra kwasa tana kallonsa ta ce""'' 😌😌😌😁 Mun shiga uku😤😤😤😤 *wollah in fada maku na ci waya, sai dai a yi hakuri har mu samu daidaito da ita ko na cenza wata, thank you* 😔😔😔😔😔😔😔😔 💔💔💔💔❤‍🩹❤‍🩹💔💔💔💔 *DA CIWO A ZUCIYATA* 💔💔💔💔❤‍🩹❤‍🩹💔💔💔💔 _MALLAKIN_ *SAJIDA NIJAR* *FREE BOOK NE* 💓2️⃣7️⃣ LITATAFAN MARUBUCIYAR Duk karyar kada Yar mahaukaciya Neman na kaina Bani da zabi Bak'a ce Kutkale Makauniya ce Mage Duk nisan jifa Idan ka raina inda kake Dutse Alkalamin kadarata Bani da zabi Dakika Biyar Now *Da CIWO A ZUCIYATA* *Tallah, tallah, tallah* *SECRET DE LA FEMME DU MANGA* _Gidan Kamshi, Sirrin Manyan Mata, nesa tazo kusa,Amarya ,Uwar gida,Ango da mai gida Har ma da yan mata da samari shin kuna sane da cewa HAJIYA FUSAM ta shirya tsaf domin gwangwaje ku da turarakunta masu dankaran kamshi? Tare Kayan gyaram jiki na musamman ,wanda daga nesa kamshin ki kadai ya wadatar ya isar da sakon zuwanki waje,gidan ki kuwa sai ya zam abun kwatance wajen kamshi, kar na cika ku da surutu bara in fara zayyano su_ Farar Humura Bakar Humura Humura special, humura de bain Humura epicé Lait de nuit Parfums désodorisant Parfums rideau et dras Lait de nuit Alkam Kulakcam *Waɗannan kadan ne daga bangaren turaran ruwa* Gagab, sandal flex, Durot, durus, sandal fleur, tafarce, farce, sandal bangui, sandal, hypotonic sandal, al'ut, coktail creation VIP, Gajiji, Mankaji, turaran wutar labule da cafet, Aba malan, boulettes *Munada bangaren gyaran jiki kamar haka:* mai mai saka santsin jiki, mai mai kanshi, Kayan gyaran jiki mai saka fata ta yi santsi da laushi, kayan gyaran jiki mai saka fata ta yi fari, Sabulu mai saka fata ta yi haske, sabulu mai saka fata ta yi santsi, sabulu mai goge yanayin fata, mai wanda baya saka fari mai gyara fata Sayen na gari mai da kudi gida,sai an gwada akan san na kwarai💃💃 Hajiya Fusam na zaune a kasar Niger domin yin magana da ita kai tsaye tuntuɓi wannan number 97 82 44 94 *SECRET DE LA FEMME DU MANGA* Gidan Kamshi, Sirrin Manyan Mata💃💃💃💃💃 Tana kallonsa a saman lebenta ta iya furta" TAUFEEK?" sai dai mikewar da ta so yi bata samu yi ba wanda ke gefenta ya kama mayafinta ya maidata zaune saman kujerar kamar wani wanda ya santa ko suka yi sabo da shi, shi kuwa tunda ya zauna addu'a ce yake yi a kasan zuciyarsa kan Allah ya sa a dauke su summa su samu wannan dace na kasance ma'aikatan wannan asibiti mai daraja A hankali ya dauke dubansa ya sake tsayawa cirr a gabansu baki daya kafin ya bude bakinsa Cikin gogagen turanci, turanci irin na gogagun wa'inda suka koye shi har suka so su fi mai kora shafawa, watau su fi turawan iyawa domin nasu turancin na haihuwa ne sukan iya yinsa yadda suka yi niya koda basu ba komai hakinsa ba Da salama ya fara yi, wata salama irin ta nagartatun yan gayun nan, sannan ya fuskance su ya shiga bayanin abinda ya tara su a wajen Ba alamun wasa ko zolaya a tsakaninsa da su ya ce" Kamar yadfa kuka sani a wajen aiki bana wasa bana son a min wasa dan abu kalilin na iya aika mutun kiyama idan har ka yi wasan, hakan ya sa nake aiki ba sani ba sabo, in ka iya mu yi, idan baka iya ba ka koma ka koya!, Ina fatan du kun san haduwar nan na daya daga cikin abinda yake wajibi a garemu du karshen wata? " Kusan a tare suka amsa da yes sir Hakan ya saka shi dan yin murmushi sannan ya juya ya koma wajen abokan aikinsa ba tare da ya sake furta A ba A lokacin ne Chef ya karaso gabansu ya dora daga inda ya tsaya ta hanyar gabatar masu da wanene shi, watau shi wanda ya tsaya ya yi magana a gabansu a yanzu da kuma sauran ma'aikatan da suka shigo tare A hankali suka shiga gabatar da rabe rabe dan kowani Likita da wa'inda zai yi evaluer , shi kuwa yana tsaye gaban teburin nan tsayuwa irin ta watsa kafa kadan, hannunsa na hagu cikin aljihun rigarsa ta likita wace ya kai sau uku Chef na sake kallon yannayin nan da alamun mamaki a fuskarsa, domin haka din nan da sir ya yi shine da kansa ya hanna cewar ina likita ina tsaye tsayen saka hannu a aljihu idan Kanada abin yi gwara ka yi da ka zo kana tunani a kan aiki, sai kuma ya ga ya dan dantse lebe sannan ya saki, hakan ya tabatar masa ko menene yau sir akoy abinda ya tabo shi ko yake shirin tabo shin Mintina ƙalilan macen ta sanar masa sun daidaita komai, dan haka ya karasa shima wajen zamansa ya zauna sannan ya sake zuba ido sosai da sosai a kan harkar aikin A hankali ta juyo dubanta daga kansa ta kalli Wannan bakon da suke tare a lokacin da ya rage muryarsa ainun ya ce " sister ko dai baki da lafiya ne? Na ga tun dazun kin yi wani iri kuma sir kike kallo, ki dan maido hankalinki nan idan an gama da su za'ai mana kuma mu fa shine zai yi mana ance baya bari wani ya daukar masa ma'aikata sai ya gamsu da iyawarka yake daukan ka" A hankali , kamar wace take koyon juyar da kai ko motsi da kai ta juya daga fuskar bawan Allahn nan ta sake kai dubanta wajen da kwakwaluwarta ta toshe harma take son Sannin wanene wannan bawan Allahn Ido hudu suka yi, idannuwanta a cikin nasa A hankali ya sake zuba idannuwan nata tana kallon nasa, da wani duba kamar wace ke son sai ta ga wani abu da ta sani a cikin idannuwansa, sai dai wani yannayi na bacin rai da take karantawa a idannuwan nasa ya sakata dauke dubanta ta juyo wajen bawan Allahn nan wanda ga dukkan alamu zai yi dan surutu dan sunna kuskus da na kusa da shi ne A hankali ta mika hannunta ta tabo farar rigar dake jikinsa dan ba zata iya masa magana ba, gashi maganar tasu kamar ta kurame ne dan ba mai daga sautinsa kowa na dan abinda ya fi tsaye masa a rai ne cen ciki ciki kamar munafukai Muryarta a shake ta ce" To ama, wannan din wanene shi?" Ido ya dan zarro da dan mamaki a kwonce saman fuskarsa ya ce" Baki san professeur Mai kwano ba?......." Gabanta ya yanke ya bada wani irin karan da kunnayenta da zuciyarta ne kawai suka iya ji A hankali ya ce" Ama bakya kai ziyara manyan asibiti ko?, Wannan yanzu baki sanshi ba a matsayinki na likita? Ai ko patient sun san shi, dan da kika ganshi nan a kasar nan shine yaron da ya fara zama professeur a fannin aikin zuciya da kannanun shekaru, dan yadda mahaifiyata ta fada min a shekara talatin da takwas tuni ya fito a rikake jajirtacen likita, ke dai Allah ya sa munada rabo , in muka samu an gama...." Da sauri ta kifta idannuwanta, shekara talatin da takwas....., No ba TAUFEEK dinta bane, ba nata bane, TAUFEEK dinta ai shekarunsa dududu basu wuce talatin ba, kuma TAUFEEK dinta dalibi ne, bayan wannanma yau ta san TAUFEEK da har zai bace mata????....., Dan haka da har kwarin gwuiwa ta ce" Wai meye sunnansa complet" *"Mai kwanoni ELHAJ Zakari Muhammad TAUFEEK"* ya fada cike da begen sunnan kansa yana kai dubansa bangaren da TAUFEEK din ke zaune Da sauri ya dan zarro ido ya juya ya gyara zamansa yana kimtsa kansa ɗan sai ya ga kamar su Sir ke kallo Tunda ya fadi sunnan nan, na mutumen da ta sani a matsayin TAUFEEK ZAKARI wanda sai daga baya bayan shekaru biyu da sanninsa ta san d'a ne a wajen Mai Kwanoni har ta san gidansu ta san ahalinsa sai kanta ya fara hade mata abubuwa sala sala ta yadda ta shiga tunani mai tsauri da nisan gaske har ta daina jin motsi da fahimtar abinda ake yi ta afka a tunanin me kennan? Me hakan yake nufi kennan? Menene wannan din kennan? TAUFEEK dinta? TAUFEEK din da iyayenta suka sani matsayin baban amini kuma abokinta?, Taufeek din da sai dai ta daki kirji ta fadi wanene shi wa duniya? TAUFEEK din dake kare mutuncinta su hau sama su fado su shirya? Taufeek din da yake tamkar wani babi na rayuwarta wanda take jin ba zata iya shaƙar numfashi ba tare da zumunci da shi ba?, Shi din nan da a cikin sirrin rayuwarta wanda Mamanta bata sani ba shi ya sani? Shine tsaye cen a matsayin bako sabon bako a duniyarta da rayuwarta baki daya? Sai Khausar ta tsinci tunaninta na hade mata , domin tashi daya sai ta shiga tunanin to anya a tarenta da shi akoy abu daya da ta sani gaskiya? Kar aje ahalinsama da ta sani ba nasa bane, kar aje Mama ba mamansa nace, kar aje Hajia ba kakarsa bace, kar aje, kar aje kar aje.................... Harta shi din kansa lokaci daya tsoro ya shige cikin zuciyarta cewa kar aje aljani ne ya shiga jikinsu ita da iyayenta yake mu'amalar zumunci da su....., Kai hatta rashin samun mijinta sai da ya gifta a kwakwaluwarta cewar kar aje to aljanun a jikinta ne suke??......babu dai abinda bata saka a ranta ba, wa'inda burinta ta samu kanta gaban mahaifiya, mahaifiyarta kadai ce zata iya warware mata wannan rudani da tashin hankali Ta matukar shagala a tunaninta ta ji an sauke hannu kan hannunta Da sauri ta kalli wanda ya tabata, wannan suarayin dai ne, watau ta tabo shi dazu shine shima ya tabata yanzu tabawa irin wannan domin hannunta ya taba kai tsaye sannan da ido ya mata alamun ta mike mana Mikewa ta yi, kaffafuwanta na son gaza daukarta ta zuba dubanta a kansu su biyu Shi sir din, sai likitar mace wace ke sanye da farin glasss fara kal da ita da hakoran makarta biyu sai walwali suke ta dan zubawa yannayin Khausar din ido ta ce" Lafiya kike?" Khausar ta hadiye wani irin yawu mai wuyar fasara kafin ta iya amsawa cewar kalau take Kacokam ta maida hankalinta kan likitar nan, wace ta fara yi masu Barka da zuwa cikin mutuntasu ba da wulakanci ba, sannan ta shiga kwatanta masu yadda nasu gwajin zai kasance, yau rana ce ta farko zasu fara amsa tambayoyi ne a kan theori zuwa gobe wa'inda suka wuce sai su samu damar zuwa gabatar da pratical dinsu Sosai suka bata hankalinsu, cikin nutsuwa a tsayen nan tamkar tashin hankali ta ringa jefo tambaya sai ta zabi wanda ta yi niya ya bata amsa, a kadan sai ta maka tambayoyi kusan goma kana bada amsa shi kuwa yana tsaye yana bi da kallo yana kuma rubutawa a wani litafi a hannunsa har aka zo kan khausar Cikin ikon Allah a Tambayoyinta daya ce kawai bata amsa ba, itama ba sanninta bane bata yi ba, asalima shi likitan shine ya mata tambayar cikin Muryar nan tasa ta tsare gida da harare harare irin na manyan mutane a waje din nan , sai kawai ta samu kanta da zubawa fuskarsa ido har sai da ya cire nasa duban ya ba likitar damar yi mata tambaya sannan kiri kiri ya dora bata bada amsar wannan tambayar da ya yi ba Ita dai likitar Tambayoyinta take yi har suka gama da su sannan aka umarcesu kan su je cafetariat su karya, zuwa karfe uku su dawo su duba sakamakonsu , du wanda ya samu gobe karfe bakwai ya samu isowa dan fara aiki Da wannan suka fice, har ta kusan fita ta sake dakatawa ta juyo, yanzunma ita yake kallo, da kallon nan nasa wanda idan tana masa fada yake zuba mata ido ya yi ta binta da shi A hankali ta lumshe idannuwanta wasu irin hawaye suka nemi saukowa daga gurbin idnanuwan nata Da sauri ta cire kanta ta fice ta bi ayarin sababin mutanen da za'a daukan suka sauka Sam Khausar sai ta kasa binsu wajen cin abincin Asalima du gaba suka sakata sunna mata tambayar yaya za'a yi ta tsare sir da ido yana magana ta ki bada amsa?, Ta kuwa san wanene shi? Bafa ya son haka, idanma birgeta ya yi ta yi gagawar cire wannan tunanin a ranta dan kuwa tsaf zata iya hadiye zuciya ta mutu tana ji tana gani, domin dubunta sun rasa aikinsu saboda nacin sunna sonsa, wasun na nan cikin wahalar nuna masa soyaya, abubuwa dai gasunnan ba dadin ji a wajenta ita, saima kunya da ta ringa cike dukkan wani gaba na jikinta, a dole ta nuna masu cewar zata zauna a filin asibitin bata jin yunwa, da wannan suka shige suka barta sunna tayata aduar Allah ya sa kar ta jawa kanta saboda ta tsaya wasa a lokacin da ba'a masa wasa Tana nan zaune sallah kawai take mikewa ta je ta yi a masallacin mata sannan ta dawo ta zauna har suka haura suka dubo result din, cikin ikon Allah a cikinsu babu wanda ba'a dauka ba, domin tana nan zaune suka kawo mata result din ta bi da kallo sunnanta ne na karshe a kafe a result din, ta yi dan murmushin yake suka zauna tare sunna dan zantawa da musayar numbo har yama ta yi sosai du suka mike kowa ya kama gabansa A hankali take tafia, bayan tarin tunani mai kasara zuciya da kwakwaluwa tana tare ne da tarin yinwa da gajiya, dan abincin da ta ci tunda duku duku babu shi a cikinta, Tsabar a rude take sai da ta karasa wajen ajiyar motoci zata ratsa ta wuce ta tuna tana da dan sahu, dan haka ta rakube jikin wata mota mai numfashi ta ciro sabuwar wayarta yar karama ta shiga kiran mai adaiditar A kira na biyu ya daga yana bata hakurin bai daga da wuri ba Murya a matukar sanyaye ta ce" Mun tashi" Mai adaidaitar ya shaida mata cewa gayanan zuwa Wayar ta kashe ta dan sake jinginar da bayanta jikin motar tana sauke ajiyar zuciya hadi da sada kanta kasa A hankali kunnayenta ke jiyo mata takun mutane, da budewar mota da tashinta da tafia, har ta ji kamar ba kowa zuwa yanzun A hankali hancinta ke son shaƙar mata kanshin turaran da itace ta bashi shi da kanta matsayin gift din aurensa tun daga lokacin idan ya kare sai ya saka ta kawo masa wani bata san dadinsa yake ji ko me ba Bayan jin kanshin a daf da ita, sai ta fara jin alamun innuwar mutun, sai kuma idannuwanta suka sauka a bakake sidik din takalman ƙafarsa sau ciki masu masifar kyau da daukan ido Da rashin kwarin gwuiwa ta dago dubanta ta sauke a saman fuskarsa, lokaci daya shi ya lumshe nasa idannuwan a hankali ya budi bakinsa ya ce" KHAUSAR......." Da sauri ta sake bin bakin nasa da kallo.. .., eh Khausar ya fada , ita dai Khausar A hankali TAUFEEK ya dan sake dubanta ya ce " Khausar Please, ki daina alamun nan na ranki a bace, tun dazu nake kallonki, ki daina min kallon kamar wani bakinki ko wanda ya maki karya, ki tsaya na fahimtar da ke abinda kike tunanin na boye maki kin ji?????"...... Ya fada, da sanyayar Muryar da ta san shi, Muryar da ta san TAUFEEK dinta da shi, Taufeek din mafarkin ta, ko tace aljannin tunaninta Da sauri ta kuma cire dubanta a kansa ta juya da nufin tafia............... Taku biyu ya yi ya riko mayafinta, hakan ya sa mayafin nata faduwa gaba daya daga jikinta daga yafen da ta masa Ransa ne ya ji ya fara ɓaci, ya bi mayafin da kallo a hannunsa a lokacin da ta juyo da nufin amshe mayafinta ta yi tafiyarta ba tare da ta ce da wannan aljanin ci kanka ba, dan kuwa yanzun zata tafiyarta a kafarta ne ta sanarwa mama a yi gagawar kiran Aba a fada masa ya dawo du inda yake a mata rukiya, dan ta gama yarda ta jima a duniyar aljannu har ta janyo iyayenta ciki bata sani ba! "Wannan din wace irin banzar dabi'a ce kike son dauka bayan kin san na hanna? Meye ya sa kika yafa wannan abin kika zo har nan da shi? Bayan wannan kika zo kina kallo saurayin nan na taba maki hannu ba zaki iya hannawa ba? Menene wannan sabuwar dabi'ar da ba taki ba? Bafa na son haka kin sani sarai?" Ya fada yana huci daf da ita irin yadda suka saba idan ta bata masa Gaba daya Khausar sai ta karra tsorata, hawayenta suka bale, sai ta ringa hasko abin ta wata fuska daban.....ta yiwuma bakin aljani ne ya aureta tunda har yana mata kashedin wani ya taba ta Rai bace ta nuna shi tana zarro idannuwanta ta ce" Ka min shiru malan, ka min shiru ka ji? A'uzubilahi mina shaidanin rajin! Ba alaka tsakanina da kai ba zumunci ba fahimta bale wani abin ya shiga tsakanina da kai! Ka yi nesa da Ni daga yau na gane kai aljani ne ba Ni ba kai! Oh ni ga mahaukaciya ko? Ga shashasha! To ka shani daya ba dadi yau zan fadawa su Mama aljani kake macuci, ka je danginka ka bi ba dai Khausar ba, kuma hijab an ki ba'a sakawa, maganar wani ya riken hannu me kake nufi, kai jinsin aljani zaka rike min? An rike min hannun an kuma ka yi turnukin hayaki ka shakeni na mutu in gani!, Kuma bari ka ji ko a waya na kiranka sai na sauke maka wala ya'uduhu yifzuhma!, Bayan wannan in ka kuma zuwa anguwarmu a siffar dan Adam dan annabi sai mun tara jama'a mun kone ka, shirme Ni zaka haukata? Wa bilahilazi baka isa ba!" Ta karashe fadi tana wartar mayafinta da dukkan karfin da ALLAH ya bata, sai dai ga dukkan alamu kamar ta dan shafa mayafin ne dan ko alamar fita daga hannunsa bai yi ba A tsorace ta dan ja baya sakamakon kallon da yake mata wanda ya kayar mata da gaba Da sauri ta waiwaya wajen wani vigil da ya karaso jin hayaniya sama sama dan gannin ko waye Da sauri Vigil din ya yi gagawar yin baya bayan ya fadi" Sorry sir" ya koma bakin aikinsa A birkice ta juyo tana sake kallonsa......., Sorry sir???????, Kennan yana ganninsa shima? Yana, yana?????, "Wayo allahna......" Khausar ta fada tana kokarin dora hannunta saman kanta Sai kuma ta fasa a hankali, ta matukar rage karfin muryarta, hannunta na rawa rawa ta miko da nufin taba fuskarsa Gannin bai hannata ba ya sakata kai hannun nata a hankali for the first time da ta taba fuskarsa haka a hankali ta dan shafa gefen fuskarsa mai dauke da saje madaidaici har zuwa wajen jajayen lebensa sannan ta sake zuba idannuwanta cikin nasa a hankali ta sauke dagen da ta yi dan shafa fuskar tasa ta nemi janye hannayenta zuciyarta na yayankewa tana neman sake fitar da ita daga hayacinta a raunane ta so janyewar dan ta yi tafiyarta, sai dai ya ki bata wannan damar ya saka lalausan hannunsa da sauri ya rike nata hannun ta wajen tsintsiyar hannunta a hankali ya maida hannun wajen da ta dauke, daf da lebensa yana kallonta ido cikin ido a sanyaye ainun ya ce" Please besty am, clm dwn, Khausar nine fa, TAUFEEK dinki ne......." Kai ta langwabe, hawaye suka shiga tsere a saman kuncinta, zuciyarta na dokawa da karfi , lebenta na rawa rawa tana kallon fuskarsa da ta dauki ja da idannuwansa da su dinma suka dauki jan, lebenta na barbarbar ta ce""''' Oh ya rab, du yadda na so sama maku da yawa ya gagara sorry plz😂 sai na gyara wayana wollah😒😒😒😍😍😍😍😍😍😍😍😍😍😍 Yanzu fa za'a shiga wani babin Babin rikicewar zuciya da kwakwaluwa Babin bugawar zuciya da tashin hankali A dole tauheeki jikan hajia ya yi hawaye A dole besty ta yi baram baran da kowama dan ita ba shashasha bace😒😏 A dole muma mu rikice domin ba zamu taba yarda da rikicin nan ba Abinda na sani shine ko me lukutar Aba zata yi a kan gaskiyarta take! Mu kafta auren Mujaheed da khausara yar baiwa🥹 Nnnn. 🚶🏻‍♀️🚶🏻‍♀️🚶🏻‍♀️🚶🏻‍♀️ Na tafi 💔💔💔💔❤‍🩹❤‍🩹💔💔💔💔 *DA CIWO A ZUCIYATA* 💔💔💔💔❤‍🩹❤‍🩹💔💔💔💔 _MALLAKIN_ *SAJIDA NIJAR* *FREE BOOK NE* 2️⃣8️⃣ LITATAFAN MARUBUCIYAR Duk karyar kada Yar mahaukaciya Neman na kaina Bani da zabi Bak'a ce Kutkale Makauniya ce Mage Duk nisan jifa Idan ka raina inda kake Dutse Alkalamin kadarata Bani da zabi Dakika Biyar Now *Da CIWO A ZUCIYATA* *Tallah, tallah, tallah* *SECRET DE LA FEMME DU MANGA* _Gidan Kamshi, Sirrin Manyan Mata, nesa tazo kusa,Amarya ,Uwar gida,Ango da mai gida Har ma da yan mata da samari shin kuna sane da cewa HAJIYA FUSAM ta shirya tsaf domin gwangwaje ku da turarakunta masu dankaran kamshi? Tare Kayan gyaram jiki na musamman ,wanda daga nesa kamshin ki kadai ya wadatar ya isar da sakon zuwanki waje,gidan ki kuwa sai ya zam abun kwatance wajen kamshi, kar na cika ku da surutu bara in fara zayyano su_ Farar Humura Bakar Humura Humura special, humura de bain Humura epicé Lait de nuit Parfums désodorisant Parfums rideau et dras Lait de nuit Alkam Kulakcam *Waɗannan kadan ne daga bangaren turaran ruwa* Gagab, sandal flex, Durot, durus, sandal fleur, tafarce, farce, sandal bangui, sandal, hypotonic sandal, al'ut, coktail creation VIP, Gajiji, Mankaji, turaran wutar labule da cafet, Aba malan, boulettes *Munada bangaren gyaran jiki kamar haka:* mai mai saka santsin jiki, mai mai kanshi, Kayan gyaran jiki mai saka fata ta yi santsi da laushi, kayan gyaran jiki mai saka fata ta yi fari, Sabulu mai saka fata ta yi haske, sabulu mai saka fata ta yi santsi, sabulu mai goge yanayin fata, mai wanda baya saka fari mai gyara fata Sayen na gari mai da kudi gida,sai an gwada akan san na kwarai💃💃 Hajiya Fusam na zaune a kasar Niger domin yin magana da ita kai tsaye tuntuɓi wannan number 97 82 44 94 *SECRET DE LA FEMME DU MANGA* Gidan Kamshi, Sirrin Manyan Mata💃💃💃💃💃 Lebenta na barbarbar ta ce" TAUFEEK? , Dan Allah ka sanar min kai mutun ne ko aljani?" Magana take yi ranta na kuma dugunzuma yana ɓaci, hankalinta na neman tashi, hakan ya sa take fitar da numfashinta da dan gaggawa da kuma dan karfi, wanda ya hadasa a dole numfashintan nan shine yake shaka A hankali yana rike da hannun nata yake so sai ya saka ta daina hakin nan ta hanyar tsatsareta da dubansa mai wuyar fasara Muryarsa a sanyaye ya ce" Kin gaji, ga yinwa kina ji baki ci komai ba, mu tafi gida ki ci abinci sai mu zauna mu yi magana, yaya zaki min duban aljani? Ni mutun ne kamarki, kuma wannan fuskar da kika gani itace Ni, plz ki kwontar da hankalinki mu tafi" Eh lalle ta yarda, ta fado duniyar wulakanci da rainin wayo Sai dai bata tunanin haka daga gareshi ba Da karfi ta janye hannunta zuciyarta na kunna tana kallonsa ta ce" Kana nufin, duka kaf zaman da na yi da kai shekaru uku da doriya ba kai din bane wani version na rayuwarka ta karya ne? ............" Ta karashe fada tana juyawa tana bin makeken asibitin da kallo ta juyo ta ce" Kana nufin wannan daula taka ce malakinka a matsayin shugaban wajen kuma baban likitan zuciya professeur sai kuma me???......" Ta yi wata yar dariya mai ciwo da daci ta kafe shi da ido ta ce" Kana nufin zaune da nake da kai, nake kwana ina tashi da tunanin a duniya ko yan gidanku ba kowa zai iya fadin waye kai ba kamar Ni ashe shirme nake yi, Ni din nan nice ban sanka ba.....?..., TAUFEEK ama me na maka da zafi a gidan duniya da ka shigo ka zabi shiga jikina ka yi abota da Ni ka shiga rayuwana .....me na yi ne da girman laifi haka????" "KHausar" ya fada a hankali yana dafe gaban goshinsa, ya sani ne akoy rikici a duniyarta idan ta rikice kuma shi dai kam ba'a raga masa, ama bai taba tunanin ranar da zata san waye shi zasu iya rikicewa har haka ba, abinda ya sani daya ne kwal zata sauko ta hakura kamar yadda ta saba su shirya, kai ama docter ya masa rashin mutunci, daga cewa a turata clinik sai ya turota nan? Ko bai gane yana nufin clinik dinsa ba wai Lafiya clinik ba? Gashi rana tsaka zai hadasa masa rigima da yarinyar nan! A hankali ya saki gaban goshin nasa ya fuskanceta , a tausashe ainun ya ce" Du fa ba inda kika nufa bane, Ni inspector ne a fannin bincike na abinda ya shafi lafiya, kamar yadda kika sani akoy office dake kula da hakan, na je makarantarku ne dan na bincika a kakama wa'inda ke aikata mana aiki irin na a zo rana tsaka ba'a yi shekara ta farko a dira ta biyu na, ko a tsalake ta biyun a je ta ukun, ko a ki yi sai a karshe a samu takarda, takardar karya ko ta gasken da hanyoyin da suke bi sunna samu, duka dai da sauransu....., Ai kin gane me nake nufi, ba wai karya na maki ba, kuma kin ga dole zan boye waye Ni Ko?" Da ya san abinda zai karra balowa da kyaletama ya yi ta tafin ya bita gida suka sasanta, domin a yanzun sai take gannin bakinsa, rai bace ta dakatar da shi tana fadin" Kana nufin, a zuwanka dan yin aikinka ka zo ne dan ka samu munafukan makarantarmu, sai ka taka ta kaina ka shiga jikina Ni balagazar makarantar wace take gaisawa da kowa ta san kowa take zumunci da kowa ta kuma san halin kowa dan ka cima burinka?, Wato Ni wawuyar nan wace ke iya fada maka komai Bama sai ka tambaya ba cikin saukin nan?, Ni wace bata san inda ta nufa ba da nake iya fayyace maka aikinka cikin saukin nan? Shine ka shiga jikina ka saka na sakankance harta iyayena suka sanka suke mutumtaka, ka saka na je gidanku na saki karina harda kwana Ni mai aboki dan uwa a gareni? Kana nufin a cikin aikin naka ne nake budar bakina in sanar maka matsalata a bayane ba a boye ba?, Sirrin da Umana bata sani ba a kaina ka sani, idan ina kuka burina na jika na sanar maka , ashe du rayuwar ture kake da Ni ban sani ba....? TAUFEEK ka ci amanar zumunci, kuma ba zan yafe maka ba!, Na godema Allah da na gani a yanzu ina mai tabbatar maka in sha Allah daga yanzun an gama, ko menene ya wuce, Taufeek zan ci gaba da zuwa in na samu an daukeni zan yi aikina cikin JAJIRCEWA, domin idan baka manta ba na sha fada maka ina karatu cikin JAJIRCEWA ne dan na san iyayena zasu gajiya wata rana, kanaina nice mamansu....., Zan yi aikina kamar kowace ma'aikaciya, ko ba komai a zamana da kai na karu ka taimakeni sosai cikin nuna min ba kai ka yi ba, Allah ya baka ladan haka, ama ka sani *CIWON DAKE ZUCIYATA* ya goge alakata da kai, ba zan yi zumunci da kai ba again, dan ban san yanzun a kan wani mataki za'a yishi da Ni ba, kar aje Ni din ta kaina ake bi ana cimma mutanena...." Daga haka ta sake mika hannu ta ja mayafinta, wannan karro tun kafin ta ja mayafin ya sauka daga hannunsa , ta janye a hankali ta dora shi a gefen kafadarta sannan ta juya wajen motar nan ta dauki jakarta ta rataya ta kama hanyar tafiya tana share idannuwanta har gabanta na mata ruwa ruwa kamar wace ta sha wani abu A tsaye yake, yana binta da kallo har ta bacewa ganninsa gaba daya A hankali ya dan ja numfashi a kirjinsa ya sake rintse idannuwansa ya bude ya kuma bin hanyar da ta bi da kallo A cen kasan zuciyarsa kokarinsa ya ba kansa tabacin cewa ranta ne ya baci iya bacewa shi yasa har ta yanke wannan hukuncin, ya san yadda zai bi ya bata hakuri ta sauko Dan murmushi ya yi a hankali yana juyawa dan ba sauka ya yi ba su doctors ya takawa sai ya ganta tsaye , a sanyaye ainun ya dan sake sakin murmushi, yana so lalle sai ya kori wani gefe na zuciyarsa dake fada masa kamar ba wasa take yi ta hanyar tabbatarwa ransa cewa to ai kadan daga aikinta, in dai Khausar ce idan ranta ya baci tsaf take wanke shi abinta, bata ko duban girmansa abinta, uhum abin haushi wai mayafin da ya mata magana kansa karshema a kafada ta yafa Bama rufashi ta yi ba, ai zai ga in zata iya tafiya har gida da shi a gefen kafada Yana shiga office dinsa ya ciro wayarsa ya zauna a hankali ya shiga kiran numbarta Kira na farko ya shiga, ama na biyu sai kiran ke dawo masa Ido ya dan zarro dan hakan na nufin ta saka shi a Black list kennan A hankali ya ajiye wayar yana furta " Uhum Allah shi kyauta ya shirye ki" Daga haka ya ci gaba da yan aikace aikacensa, duda hankalin nasa a rabe yanzu, ama haka ya ringa aikin dan dole ne ya gama abinda ke gabansa a yau Khausar bata isa gida ba sai kusan magariba Koda ta je ta tarda Mama bata nan ama ta Bara mata ky a makota, dan haka ta amso ta zo gida ta cenza kayanta sannan ta shiga kimtsa gidan ranta a matukar bace Tana gamawa ta dora masu yar makaroni ta koma ta zauna ita kadai tana cije lebe da kuma tarin jin haushin da ya daskare mata a cen kasan zuciyarta Yanzu ita? Kennan waye ya dauketa da mahinmanci ne a duniya bayan iyayenta? Bata taba tunanin zata iya riskar wannan gagarumar surprise daga mutun mafi kusanci da duniyarta ba irin TAUFEEK Ita fa babu wani uzuri da zai gabatar mata ko za'a fada mata ta saurara ko ta gane A zamantakewarsu ya dace ace ya fi kowa Sannin wacece ita, idan tace wacece ita tana nufin koda aikin sirri yake yi a yadda ya gama karantarta in ba dan yana anfani da ita dan cinma aikin nasa bane da ya sanar mata sirrin dake boye a tsakaninsu Ita me ta boye masa ne? Irin yadda take yiwa umarninsa biyayya kuwa tana tunanin su Aba kadai suke gaban furucinsa Wata kwafa ta yi tana amsa salamar su Salma yarinyar dake bayan layinsu ta mike daga zaunen da take a zuciyarta tana ayana' hijab ko?, Zan saka ama na rantse maka ba dai irin wancen ba, kai ba zan kuma maka biyayya ba, ba Ni ba kai! Zan kiyaye adinina ama bi izinillah nima zan dauki wasu shawarwari da ake bani a matsayina na budurwa kuma musulma dan gyaran kaina ba dan batawa ba na kasance kamar kowa!, Wani sa'in harma da gudun kar kace yace nake bulumtun nan! A yanzu ka jima baka ce ba, koda yake Bama sai na kuma haduwa da kai ba bale har ka iya bani opinion dinka a kan abinda yake nawa! Domin daga yau Ni nice Ni daya ce kuma, du wani bestyma ai cuta ce, kwarai Hajia ta yi gaskiya ashe amincinmu akoy wata a kasa? Watar kuwa ba komai bace face cuta tsagwaronta!, Wasu mutanen dai sun ji kunya' Tabarma ta shinfida masu, sunna neman zaunawa sai ga Maman ta dawo a gajiya tilis, dama daga gidan rasuwa take kuma na kusa ne sosai tarema suke da Aba, Jin rasuwar da aka yi ya sakata kin fada masu abinda ta ƙunso take jira ta sanar masu, saima ta shiga hidimarsu ba tare da ta gane cewar salmar nan wajenta ta zo ba har sai da Maman ta kireta daka ta ce" Khausar, yaya zaki bar bakuwarki zaune ita daya ne haka?" Khausar da mamaki ta ce" Mama bakuwata kuma? Na zata ko aikota aka yi wajenki?" Maman ma da mamaki ta ce" Wajena kuma? To wa zai aikota Wajena?, Da aikotan ne aka yi ai da ta sanar min ko?, Na ga tare na tardo ku kuma Ni bata nuna Wajena ta zo ba ki je ki dan saurareta mana ?" Khausar ta fito zuciyarta cike da mamaki, abinda ya sa mamakin ke damunta Salmar nan dai na farko ba sa'arta bace, dan a kadan tana iya bata shekara shida ko fiye, sannan irin rikakun yan ji da kan nan ne na anguwa wa'inda ko gaisuwarka basu cika amsawa ba don mahaifinsu na mai kudin anguwa, a gaskiya a gidansu ana fadin sun cika girman kai, kuma daga mahaifiyarsu suka dauko domin kaf layin nan da bayanshi babu wanda mahaifiyarsu ke hulɗar arziki da shi, ita ta fi karfin ajinsu, mahaifinsu dai da sauki dan shi ko me ake yi a anguwa in dai ya ji ana yi da shi yana zuwa fatiha na sunna ta aure ko zana'iza Zama ta yi yanzun du a takure ba kamar dazu da take sake ba, dan dazu a tunaninta wajen mahaifiyarta Salma ta zo Salma kam ko a yanzu da Khausar ta dawo ta zauna tsaf ta kare mata kallo,.kallo irin na son Sannin shin da gaske ƴaƴanta matar nan ta masa ne har da ya nace haka da son samun kusanci irin na zuciya da zuciya da ita ko da akace likita ce ita din yake so ta zamto a cikin ahalinsu? Dan murmushi ta yi tana mikewa ta saba jakarta a kafadarta ta yan gayu tana kallon KHausar ta ce" Sister, zan juya, ki dan ban numbarki dama fira na kawo maki" Sosai Khausar ta so cewa Fira kuma? Ta me fa? Sai dai ta kasa fada saima hijab da ta saka a shigarta dakin dan bata cika son kallo irin wannan ba a rayuwa yana damunta ainun Wayarta ta dauko ba wata damuwa ta ba Salma numbar tata harma ta dan taka mata bakin kofar gida sannan ta dawo da sauri tana ta hade rai dan a dan fitar nan ta san ta sake cirarwa kanta magana, ana iya cewa bata mu'amala da mutane talaka sai masu kudi, shi yasa batama tsaya har Salma ta shiga motarta ba ta dawo da sauri A wannan daren abincin kirki kasa ci ta yi, danma juwa ta fara nusar da ita menene yinwa, da tana iya kasa cin abincin kwata kwara dan cin amanar da akai mata, wani sashe na zuciyarta kuwa kuka yake yi sosai na decision dinta, sai dai ta ja ta tsaya zata ga waye keda iko cikin ita fa shi! ____________________________________ Karfe bakwai na safe *TAUFEEK* Zaune yake saman table yana karyawa kira shigo wayarsa, kira ne mai mahimmanci dan haka ya dan mike ya shiga amsawa, Yumnah kuwa ta bishi da wani irin sansanyan kallo tana jin wani irin nutsatsen kusancin zuci da idannuwa idan tana ta kallonsa Idannuwanta ta lumshe, tana matukar jin tarin kauna da girman mijinta a zuciyarta Dawowarsa ya sakata sake zuba masa wani shayin sannan ta koma ta zauna tana kallon yadda yake dan sha yana duban screen din wayarsa dake ajiye a saman table din Dubanta ta kai itama, sai ta ga kamar call ne yake aikawa Har zata cire kanta sai ta sake dubawa dan haka kawai ta ji idannuwanta sun sake likuwa a saman screen din wayar Da sauri ta dauke idannuwanta ta zuba a saman fuskarsa Yannayin fuskarsa sam ba walwala a tare da ita, tana fadin tun jiya kamar hankalinsa a dan rabe , kuma yanzu sai ta ga yana kiran matar da ta yi tunanin ko ta tabata ne? Watau an yi baram baram ne? Dan kuwa an jima bata ga kiranta a wayar mijinta ba Ajiyar zuciya ta sauke mai zafi a lokacin da ya gama sha ya nuna ba zai iya karyawa da wuri ba zai dan fita, sannan ya mike yana daukan rigar dake ajiye mai ruwan ashe color ta vst ya dan rayata a hannunsa na hagu da dayan hannun nasa ya dan talafota a lokacin da ta karaso tana kokarin dane damuwarta Fuskarta ya dan zubawa ido kadan, kasa kasa ya ce" Ki yi kokarin wuni a wajen hajia yau Yumnah...." Cikinta sai da ya juya daga tsayan da take, ta zata ya manta da maganar cewa ta je 5 gaisar da Hajiar da ya mata, sai gashi abin ya ce za zani harda su ta wuni a cen?, Wuni? Ita da matar nan? Tap to ita ta wuni a yaya kennan? Ai ta tabata tana iya wuni ne cikin ukuba da tsoro, matar da kowa tsoronta yake a gidan? Bale ita da ta tsaneta ƙarara? ..... gaba daya sai ta rasa kuzari har ya fice a gidan ba tare da ta tabuka abin kirki ba Saman kujera ta zauna tana sauke numfashi bayan ta dannawa mahaifiyarta kira Kamr ko yaushe jajen Khausar ne suka yi, mahaifiyarta cike da mamaki ta ce" Wai a yanzunma da yarinyar nan ta fita a makarantar su ba zata rabu da shi ba?, Alakarsu ta fara bani tsoro Yumnah" Yumnah ta share hawayen da suka tarun mata a gurbin idannuwanta a sanyaye ta ce" Mama, sai kin ga kamar ba ita a duniyar da sai kuma ki ga tana nan daram a duniyar tasa, kin ga dai an dan jima ban ji duriyarta ba, kuma bata zo gidan ba tun wancen zuwan da wancen tsohuwar ta yayabota, sai kawai dazu na ga yana ta danna mata kira da safiyar nan, Ni kam ban san wannan wace irin maya ce ba!" Mahaifiyarta ta yi dan tsai, a dan kausashe ta ce" kema sai nake gannin harda laifinki, ta yaya zaki bari yana maki kiran wata a lokacin da kike tare da shi? Wannan fa saken ki ne ba komai ba, kuma yanzu ki zo ke hankalinki a tashe nima kina tayar min da hankali, a gaskiya wannan din saken ki ne!, ya dace ki san mace kike in ta laluma ko ta tsiya ki kwatantawa mijinki idan yana gabanki kece a gabansa ba wata banza ba koda matarsa take bata da wannan hurumin in yana gabanki naki ne ke daya!, Ama sai kina wani abu kamar wace ke jin tsoronsa, in na baki shawarwari ki nunan kin dauka ama in na tambaya sai ki nunan baki yi ba zaki yi, mazan nan na zamaninmu ma ba wani cika kiyaye hakin iyali suka yi ba bale na yanzu!, Na fada maki da kirsa zamu rabata da shi ama kuma wani abin sai mun dora doka irin tamu ta mata, ki sani mace fa sarauniya ce in ta yi wasa kuwa tana iya zama bola, kuma du namijin da yace shi karya ne babu macen da ta isa ta juya shi ko wani abin karya yake Yumnah, bai dai hadu da mai juya shin ba, kar ki yarda TAUFEEK ya fi karfinki ta yadda zaki dawo kina kuka da barin jiki idan ya yi magana Ni dai na fada maki, kuma maganar zuwa wajen kakarsa ban ce ki wuni ba, ko daya ban saka ki ba, ki je ki gaisheta sama sama ki dawo dakinki ko uwarsa ban saka ki sakin jiki da ita ba bale wata kakarsa da ba sonki take yi ba ni kin ji maganata!" Daga haka ta kashe wayar tana ta bambaminta, ta bar Yumnah cikin wani dogon tunanin da sake daurar damarar yaki da duk wata halitar da zata iya zamtowa matsala a duniyarta da mijinta ko wacece! Da wuri ya iso asibitin, domin yau aikin ba iya na takarda bane na aikace ne wanda yake saka tsauri sosai a cikin lamarin A wajen ajiye motocinsa na asibitin dake gefe daban da sauran motocin manyan ma'aikatan cikin asibitin ya ajiye motarsa a hankali ya sake daukan karamar wayarsa a kasan zuciyarsa yana tunanin me kennan? Me yasa take kin daga kira harda numbar da bata sani Bama?, Bai san me yasa fushin nata ya masa katutu a cikin zuciya ba Iska ya fitar mai zafi daga bakinsa a hankali ya juya da niyar daukan bak'ar jakarsa dake ajiye dan ya fice zuwa ciki, domin tuni vigil biyu ke jira ya fito su amshi kayan hannunsa idan yana da su, ya dago dubansa a hankali dan bude motar ya fito nan ya dakata da sauri yana ruko idannuwansa ya zuba mata ido A hankali ya sake dan kifta idannuwansa yana sake dubanta dan tabbatarwa ko dai ba ita bace? , Sai dai a lokacin da ta dan dakata tana laluba yar bakar dake hannunta ta ciro karamar bak'ar wayarta ta duba kiran da shine ya yi mata shi ta katse kiran ta jefa wayar a jakar ya tabatar masa lalle wannan baiwar Allahn dake tafiya zuwa cikin asibiti da shiga irin ta riga da sket daidai da jikinta, kanta da dan karamin hijab fari kal mai dan kwaliya, sai kuma dan mayafinta siriri fari kal a gefen kadarta ta yi yafe da shi, yafe jama'a ba ta bude shi ta rufe jikinta ba, harda yar agogo siririya a hannunta baka sidik wace ta kama hannun nata ya mata wani irin sassa gwanin kyau Bai ankara da kallon da yake mata ba har sai da ta bacewa ganninsa Da mamaki ya dan dafe goshinsa a hankali ya furta" me kike nufi ne Khausar?, Baki isa ba!, Hakan ba zai taba yiwuwa ba, dan kina fushi da ni ba zaki fito a haka ba sutura ba!" 😔😕 Inaga dole sai mun hadashi da Hajia ta ce igiyar uban wa ke wuyanta? Ni dai ba luwana🤣🚶🏻‍♀️🚶🏻‍♀️🚶🏻‍♀️🚶🏻‍♀️🚶🏻‍♀️🚶🏻‍♀️ 💔💔💔💔❤‍🩹❤‍🩹💔💔💔💔 *DA CIWO A ZUCIYATA* 💔💔💔💔❤‍🩹❤‍🩹💔💔💔💔 _MALLAKIN_ *SAJIDA NIJAR* *FREE BOOK NE* 3️⃣0️⃣ *GARABASA, GARABASA, PROMOTION, PROMOTION DIN LITATAFAN MARUBUCIYAR A KAN FARASHI MAI SAUKI 1K, YAN NIJAR KUWA 1000 FRANCS CEFA* 1: Duk karyar kada 2: Yar mahaukaciya 3: Neman na kaina 4: Bani da zabi 5: Bak'a ce 6: Kutkale 7: Makauniya ce 8: Mage 9: Duk nisan jifa 10: Idan ka raina inda kake 11: Dutse 12: Alkalamin kadarata 13: Bani da zabi 14: Dakika Biyar 15:Wata kokowar 16: Aure yakin mata 17: Ni zan ladabi 18: Daga tafia daukar soja *Dukansu a kan farashi mai sauki, zaka saka dubu guda ne domin promotion ne nake yi, ka tuntubeni kan layina kamar haka +227 93 81 16 18, Sajida Nijar* Now *Da CIWO A ZUCIYATA* *Tallah, tallah, tallah* *SECRET DE LA FEMME DU MANGA* _Gidan Kamshi, Sirrin Manyan Mata, nesa tazo kusa,Amarya ,Uwar gida,Ango da mai gida Har ma da yan mata da samari shin kuna sane da cewa HAJIYA FUSAM ta shirya tsaf domin gwangwaje ku da turarakunta masu dankaran kamshi? Tare Kayan gyaram jiki na musamman ,wanda daga nesa kamshin ki kadai ya wadatar ya isar da sakon zuwanki waje,gidan ki kuwa sai ya zam abun kwatance wajen kamshi, kar na cika ku da surutu bara in fara zayyano su_ Farar Humura Bakar Humura Humura special, humura de bain Humura epicé Lait de nuit Parfums désodorisant Parfums rideau et dras Lait de nuit Alkam Kulakcam *Waɗannan kadan ne daga bangaren turaran ruwa* Gagab, sandal flex, Durot, durus, sandal fleur, tafarce, farce, sandal bangui, sandal, hypotonic sandal, al'ut, coktail creation VIP, Gajiji, Mankaji, turaran wutar labule da cafet, Aba malan, boulettes *Munada bangaren gyaran jiki kamar haka:* mai mai saka santsin jiki, mai mai kanshi, Kayan gyaran jiki mai saka fata ta yi santsi da laushi, kayan gyaran jiki mai saka fata ta yi fari, Sabulu mai saka fata ta yi haske, sabulu mai saka fata ta yi santsi, sabulu mai goge yanayin fata, mai wanda baya saka fari mai gyara fata Sayen na gari mai da kudi gida,sai an gwada akan san na kwarai💃💃 Hajiya Fusam na zaune a kasar Niger domin yin magana da ita kai tsaye tuntuɓi wannan number 97 82 44 94 *SECRET DE LA FEMME DU MANGA* Gidan Kamshi, Sirrin Manyan Mata💃💃💃💃💃 Cike da jin haushin ta ya yi kyaftu ya zauna nan ba tare da ankara da yannayin lokaci ko yannayin da yake ciki ba, shi ba aiki ba, shi ba tafia gida ba, karshema sai ya danna buton ja dake nunin idan yar fitilarsa ta bada kar a shigo office dinsa baya bukatar gannin kowa A lokacin da Khausar ta fito sauri ta ringa yi wajen saukowa daga kasa, cikin sauri ta nufi bangaren su ta shige dakin su na mata sannan ta yi bayinsu da sauri ta shiga ta rufe kafin ta karasa ta dukar da kanta jikin abin alwallah ta ringa sakin nishi a jajere a jajere, sai kuma hawayenta suka bale tamkar an bale mata su ne Bata san dalilin da ya sa take jin dacin abin har haka a ranta ba Ko ba komai ai ya nuna mata a kan aikinsa yake, kawai abinda ya sa abin ya mata ciwo ainun tunanin an wulakantata ne, an wulakanta iliminta da hankalinta A kan abu daya ta ajiye kusancin da TAUFEEK ya kirkira tsakaninsa da ita dan ta zamto balagazar makaranta wace ta san kowa take hulda da kowa ba ruwanta da ta birgeka ko ta mata kwaskwasa dan ka sota, kana iya yin firarka a gabanta dan ba abinda ya shafeta, haka mu'amalarta da malamai du irin yadda duniya ta lalace ita dai da su ido ne domin ko kucakin malami ba birgeshi zata yi ba a yadda ta gudanar da rayuwar makarantarta A dole abin ya mata ciwo mai zafin gaske A dole abin nan ya taba mata zuciya Bata san me zata ce ba, yaya zata yi, tana matukar jin ciwo mai girma a zuciyarta na irin yadda mu'alamarsu zata ruguje tana ji tana gani Sai dai rugujewar shine alkhairi dan bata ga kuma me zasu iya cewa junna a yanzu ba, ya fi karfinta ya fi karfin ajinta shi din ba abokin yinta bane, ta kowani fani idan ta duba a yanzu sai ta ga idan har ta yarda ta sakawa ranta ci gaba da shi din kamar ta cuci kanta da kanta ne A hankali ta dafe kanta hawaye take yi sosai sannan ta dafe gaban kirjinta a sanyaye ta ce" Ama da wa zan yi fira? Wa zan SANARWA damuwata?, Wa zai rarasheni? Waye zai min fada? Wanene zai ringa sakani ko hannani bayan su Mama?, Me yasa ka saka na sakankance da kai haka? Me yasa ka shiga jikina haka?, TAUFEEK baka min adalci ba, baka min adalci ba TAUFEEK, shin yaya zan ci gaba da walwala ba farin cikinka a tare da Ni? Ya Allah ka bani mafita mai sauki a cikin lamarina.........." Surutu take yi irin na zafi da ciwo a cen kasan zuciyarta....... Ta shagala sosai yar karamar wayarta ta shiga kuka a cikin aljihun rigarta Da sauri ta lalubo tana tunanin ko dan sahunta ne da ya ga shiru bata tabo shi ba har yanzu? Numbar ta zubawa ido tana kallo, domin bakuwar lamba ce a wayar Tata A hankali ta daga tana dan gyara muryarta hadi da yin salama sannan ta yi shiru "Amincin Allah ya tabata a gareki kema Likitana....." Shiru ta yi, jin Muryar namiji ne, da kuma abinda aka fada din A hankali ta dan budi bakinta ta ce" Ban gane mai maganar ba?" Dan murmushi ya yi shima ya ce" Allah sarki dama nace akoy sanyin murya matata to be in sha Allah, jiya na turo kanwata Salma ta amsar min numbar dan na yi na yi na tareki na amsa na kula da wahala fa ki saurareni a hanya, karma aje ki ce min bakya so na na suma dan firgici" A hankali Khausar ke dan sauke numfashinta, lokaci daya ta afka wata sabuwar duniya ta tunani da tarin mamaki Yayan Salma?, To wane? Salma dai Salma? Kai, anya kuwa? Har yake kiranta da matarsa? Ko dai ya yi batan numba ne?, Da wahala in ba batan numba ya yi ba, ya rab........., Sai dai du rikicewar ta wannan karron sai ta ki kashe kiran haka kuma ta kasa yin wata magana da zai iya jin ba dadi Ko ba komai tana kan gaba ne ta nema irin wannan A hankali ta dan sauke numfashi jin yana ta afkin fadin ta amsa shi plz A sanyaye sosai ta dan ja numfashi ta ce" Zan je gida ne na ga dan sahuna na kira" Shima a sanyayen ya ce" Ba damuwa, sai kin zo, plz ki kular min da kanki, sannan zan yi kira idan kin huta dan ina so ki amsheni, ki dubeni ki bani dama kin ji kanwata????" Murmushi ta samu kanta da saki a hankali ta furta" Na gode" Sannan ta kashe kiran tana dan samun kanta da sake sakin murmushi Yayan Salma? Yayunta maza biyu ta sani.....shin wanene a cikinsu?................haka kawai ta tsinci zuciyarta da jin nutsuwa da farin ciki harma ta wanke fuskarta ta fito ta cire rigarta ta nade ta saka a jaka sannan ta dauki kayanta da mayafin nan nata ta kade ta dora a kafadarta tana turo baki cike da jin haushin furucinsa wai wani bata yi kyau ba, kar ta yin, karma ta yin! Ai dama ba cewa ta yi ita mai kyau bace, kwaliya ne yace itama ta aura irin na yan mata!........... Haka ta yi ta fadanta a zuciyarta har ta samu ta fada adaidaitar, domin ba wani a sake take ba da mayafin nan, kawai rikici ne rigima ce, kuma tunda ta yafa shi mamama da mamaki tace a haka zata tafi ne? Tace eh, mama ta ce da ta bude shi ta dan yafa jikinta duka sai tace ai ba komai , ita dai Mama kallonta ta yi tana jira ta ga da gaske? Sai kuwa ta ga da gasken ta tafi da yafen, jirantama tane yi a gidan ta dawo su zauna dan ba dabiar kirki bane hakan sam Rai bace Taufeek ya dawo gida, domin kowa bai je nema ba dan a sama sama yake ba zai iya jure wani neman fitinan ba, direct bangarensa ya nufa yana mai kokarin kawar da dukkan wani bacin rai dake taso masa ko dan kar ya shiga hakkin abokiyar zamansa, domin ba ita ta hasala shi ba idan ya sauke mata fushinsa bai yi mata adalci ba Sai da ya yi wanka ya sauko sakamakon irin yadda ta yi ta kai kawo cewar abincinsa na jiransa Zama ya yi saman cafet a hankali ya mika hannu ya kashe tv dake yi, domin baya son hayaniya ne sam, kansa na dan masa ciwo, gaba daya ransa a dagule yake, sai dai abu daya da ya sani shine ba damuwa ya kyaleta, zumunci ne tunda ta katse babu yadda zai yi, ba zai saka mata wuka a wuyanta ba kan dole sai ta yi zumunci da shi tunda bata ra'ayi, yaya zata kasa yi masa uzuri a kan abinda yake aiki ne nasa? Idan ta ji cewa Yumnahma bata san komai game da aikinsa ba a matsayin dan kasuwa kuma matashin dan makaranta ta san shi ta ce me kennan? Ya dace ta masa uzuri, yaya take tunanin zai fito ya ringa yayata mata maganar sirrin aikin da yake da girma da daraja irin ta taimakon rayuwar dan adam?, Itama da gangan ta kasa gane cewa ya jima da samun takarda irin tata take tafe a makance, da gangan ta ki fahimta dan kawai ta daga masa hankali, kuma ta taki Sa'a ta daga masan domin ta fado a daidai lokacin da ta riga ta gama zamtowa tamkar jinnin jikinsa, yar uwarsa ta jinni, ama kuma ba komai dan uwankama yana iya kinka ka rayu kuwa ! Abincin ya ba hankalinsa bayan ya budi baki da kula ya ce da ita" Thank you" sannan ya yi bismillah ya dan fara tsakura Ya koro da tabawar ya ji du ya koshi, a dole ya mayar gefe ya dan dauki jus din kwalba da ta zuba zai kai bakinsa yace" kin je kin wuni a bangaren na Hajia?" Sai da gabanta ya fadi jin tambayar da ya yi mata, sai dai ta Basar cikin kisarta ta ce" na je , eh na je" Yannayin da ta dan sosa gaban goshi ya bi da kallo , kasa kasa ya ce" ina nufin kin wuni a cen din ne?" "Aa ban wuni ba, ama a kalla na kai minti ashirin......." Ta fada cike da tabbatarwa kanta ai ba zai yi fushi ba tunda ta je din Jus din ya ajiye yana binta da kallon mamaki A tsanake ya ce" kina so ki ce min umarnin da na baki ki je ki wuni da Hajia baki cika ba?" Da sauri ta dago dan jin yannayin amon muryarsa ya cenza daga laushi laushi zuwa yannayi mai zafi zafi Rai bace ya dan sake dubanta ido cikin ido ya ce" Wannan din ya zamto na farko kuma na karshe, da zaki take umarnina, idan nace kaza za'a yi shi za'a yi! Sannan ki kula ki kiyaye mutuncin dangina ta haka ne zan iya mutunta naki, Hajia kakata ce, ki kula, ki bata girman da take da shi idan ba haka ba bana tunanin in har zamu iya fahimtar junna!" Daga haka ya mike ya bara mata jus din gaba dayama ya fice a falon Hankalinta sosai ya nemi barin jikinta, lokaci daya jikinta ya dauki rawa ta rasa yaya zata yi, ya fi a irga tana gwada bin bayansa tana komawa dan ta ga ya nufi bangaren Hajia, karshe dai nan ta zauna ta zuba uban tagumi tana gadin dawowarsa dan ta bashi hakuri, in dai wajen hajia ne zata je zata je ta labe har yama ta yi ta dawo dan ba zata iya zama su shaki iska daya da hajiar nan ta kasheta a banza a wofi ba Tunda ya shigo bangaren Hajia ya nemi waje ya zauna ya hade gabas da yama bai ce da ita ufan ba har ta zo da kaskon turare turaranta ta ce" Gaba daya ka fara aiki irin na wa'inda basu cika jin tsoron Allah ba magidanci, yanzu yau kwana biyu fa ban maka turare ba, Ni kuma ba zan ba wancen muciya da zanin kayan tsarinka ta je ta cenza da yan barbade barbade na matan zamani a malake min jika a sakani uku, gyara zamanka dan dage rigar nan na shafa maka a bayan cikinka wannan akace sunnansa kaikayi koma kan mashekiya, du wanda ya nufeka da asiri in sha Allahu zai kome masa ne, gyara da kyau mana wai meye kake cika kunci uwa balan balan" Karra hade fuska ya yi ya ce" Kar ki saki ki turara min kaurin nan ke kuma!" Hajia ta yi turus tana kallonsa, kasa kasa ta ce" Magidanci maganin tsarin ne ya zama kauri kuma?" Cire kai ya yi bai bata amsa ba, hakan ya sa ta ajiye tana kallonsa ta ce" Kai ko wancen mai kai uwa na ifirutun ce ta bata maka? Ka dan yar nan dan rashin da'a da ta zo gaisheni kafada da kafada muka gaisa? Yar nan ka kuwa san in ta je cen bata zuwa bangaren Mamanka sai dai na kishiyoyi? Ka fa ja mata kunne dan Ni nan ko mai kwanoni ya yi kadan bale matar dansa, aikin banza aikin wofi " "Ki matsa min da warin abin nan nace, kuma ki daina sako ubana a abinki kin dai ji na fada maki, da kike cewa wai tsoron Allah in tambayekima hijab umarnin Allah ne ko na mutun?" Hajia ta yi tsuru tana gannin yadda fuskarsa ke Dada daukan ja alamun rikici ke kunne a cikinta na kirki, gaba daya sai ta bace, to waye kuma ya ki saka hijab ne? Me ya kawo maganar hijab ne? Mema aka yi da maganar hijab ne? Ita dai tana iyaa rantsewa da huwa rahamanu a shigowar magidanci bata kawo maganar hijab ba ko daya, to wa ya kawo maganar hijab? Kaskon ta mayar gefe ta bada abin a ranta tana ayana' ai da yake fanka a kunne ta kado maka iskar, bari in ji ubanda ya taba min kai yau sai inda karfina ya kare dan ba zai yiwu ba gaskiya ina zaune a ringa kokarin dagan hankali ana kawowa magidanci farmaki!' A fili kuwa ta dube shi ta ce" To wai wani shedanin ne yace kar a saka hijab? Ai du wanda ma ya ki hijab gaskiya shedani ne, bayan wannan ai shi lulubi dadi gareshi, me ake da gayar zirr ba auki? Na tabata wancen hure ka fadin ce bata son saka hijab ko? To ta kiyayi duniya ta kuma kiyayeni dan bata isa ta daga hankalin jikana ba tashi mu je in ji uban me take son budewa da ba zata saka hijab ba a bushe kamas, yo in bandama son duniya ke matar aure me kuma ya rage ? Tashi mu je in ci duniyar uwayenta a dakin cen yau in ban mareta ba ba Ni na haifi mai kwanoni ba!" Tunda ta fara hayagahar kawai ya yi tsai yana tunanin duniya, shi dai ya ga abu gannin idannuwansa, to kuwa zai tabatar mata maganarta ake ita din nan ba kowa ba, dan haka ya sake hade gira ya ce" ba wani inda zamu je, kina neman wanda ya hanna saka hijab aka zo kanki an tsaya, maganar jin tsoron Allah kuwa ki yiwa kanki fada! Kina zaune sai neman fitina !" Hajia ta yi tsuru tana kallonsa, to ita yau wani dan bakin ciki ne ya hadata fada da jikanta? Gashi dai a sanninta ba abinda ta masa ama tunda ya shigo kamar wanda yake jin haushinta Murya a sanyaye ta ce" Wai waye ya taboka? Ni kuma wa na hanna saka hijab a duniyar nan ta malikiyau midini?" 😤😤😤😤😤 Gaskiya gaskiya dan gidan mai langa ya fara kin jin tsoron Allah, wannan hali sam ba na Musulmin kirki bane, mema Hajiar ta yi da zaka nemi dora Mata laifi? Ka ji tsoron Allah 🙄🙄🙄🙄😏 *GARABASA, GARABASA, PROMOTION, PROMOTION DIN LITATAFAN MARUBUCIYAR A KAN FARASHI MAI SAUKI 1K, YAN NIJAR KUWA 1000 FRANCS CEFA* 1: Duk karyar kada 2: Yar mahaukaciya 3: Neman na kaina 4: Bani da zabi 5: Bak'a ce 6: Kutkale 7: Makauniya ce 8: Mage 9: Duk nisan jifa 10: Idan ka raina inda kake 11: Dutse 12: Alkalamin kadarata 13: Bani da zabi 14: Dakika Biyar 15:Wata kokowar 16: Aure yakin mata 17: Ni zan ladabi 18: Daga tafia daukar soja *Dukansu a kan farashi mai sauki, zaka saka dubu guda ne domin promotion ne nake yi, ka tuntubeni kan layina kamar haka +227 93 81 16 18, Sajida Nijar* *LITAFIN KWATENA* 👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨 *BAIWATA* 👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨👩‍❤️‍👨 Alhamdulillah, Alhamdulillah, labarin BAIWATA labari ne da zan iya kiran sa da BAKANDAMIYA, sakamakon ƙayatuwar labarin, y yi nasarar lashe gasar Gwarazan HIKAYATA, wanda ya zo ɗaya a cikin labarai guda goma da aka zaɓesu kuma za'a bugasu a takarda (publish). Ganin wannan gagarumar nasara da muka fara hayewa yasa muke da ƙudirin rarraba littafin gidajen radio da muke da su dan su karanta da kuma bayar da kasuwarshi ga masu sana'ar siyar da littafi. Sai dai hakan ba zai faru ba sai da *gudumuwarku masoya*, ƙauna da taimakon da zaku mana shine, ku siyi littafin na takarda duk da na san dayawanku kun karantashi sannan free book ne, amma wannan zaku mana ne a matsayin gudumawarku, madadin mu ce muna roƙonku da ku taimaka ku mana karo-karo, Shiyasa muka ga Gwara ku siyi littafin ya zama guminmu ne zamu ci. _Da wannan muke roƙon da ku siyi littafin BAIWATA na takarda, nasan dayawa kun san labarin, sannan kun san ingancinsa da kuma cncantarsa, ga duk wacce ta shirya siya ta tuntuɓi wannan lambar ta WhatsApp *+227-93-81-16-18* ko kuma *+227-82-21-91-74*, farashin *1000k* ne ga mutanen mu na Nijeriya, namu na Niger kuma *1000f*. 😌 *MUNA DA YAƘINI A KANKU.* 💔💔💔💔❤‍🩹❤‍🩹💔💔💔💔 *DA CIWO A ZUCIYATA* 💔💔💔💔❤‍🩹❤‍🩹💔💔💔💔 _MALLAKIN_ *SAJIDA NIJAR* *FREE BOOK NE* 3️⃣1️⃣ *GARABASA, GARABASA, PROMOTION, PROMOTION DIN LITATAFAN MARUBUCIYAR A KAN FARASHI MAI SAUKI 1K, YAN NIJAR KUWA 1000 FRANCS CEFA* 1: Duk karyar kada 2: Yar mahaukaciya 3: Neman na kaina 4: Bani da zabi 5: Bak'a ce 6: Kutkale 7: Makauniya ce 8: Mage 9: Duk nisan jifa 10: Idan ka raina inda kake 11: Dutse 12: Alkalamin kadarata 13: Bani da zabi 14: Dakika Biyar 15:Wata kokowar 16: Aure yakin mata 17: Ni zan ladabi 18: Daga tafia daukar soja *Dukansu a kan farashi mai sauki, zaka saka dubu guda ne domin promotion ne nake yi, ka tuntubeni kan layina kamar haka +227 93 81 16 18, Sajida Nijar* Now *Da CIWO A ZUCIYATA* *Tallah, tallah, tallah* *SECRET DE LA FEMME DU MANGA* _Gidan Kamshi, Sirrin Manyan Mata, nesa tazo kusa,Amarya ,Uwar gida,Ango da mai gida Har ma da yan mata da samari shin kuna sane da cewa HAJIYA FUSAM ta shirya tsaf domin gwangwaje ku da turarakunta masu dankaran kamshi? Tare Kayan gyaram jiki na musamman ,wanda daga nesa kamshin ki kadai ya wadatar ya isar da sakon zuwanki waje,gidan ki kuwa sai ya zam abun kwatance wajen kamshi, kar na cika ku da surutu bara in fara zayyano su_ Farar Humura Bakar Humura Humura special, humura de bain Humura epicé Lait de nuit Parfums désodorisant Parfums rideau et dras Lait de nuit Alkam Kulakcam *Waɗannan kadan ne daga bangaren turaran ruwa* Gagab, sandal flex, Durot, durus, sandal fleur, tafarce, farce, sandal bangui, sandal, hypotonic sandal, al'ut, coktail creation VIP, Gajiji, Mankaji, turaran wutar labule da cafet, Aba malan, boulettes *Munada bangaren gyaran jiki kamar haka:* mai mai saka santsin jiki, mai mai kanshi, Kayan gyaran jiki mai saka fata ta yi santsi da laushi, kayan gyaran jiki mai saka fata ta yi fari, Sabulu mai saka fata ta yi haske, sabulu mai saka fata ta yi santsi, sabulu mai goge yanayin fata, mai wanda baya saka fari mai gyara fata Sayen na gari mai da kudi gida,sai an gwada akan san na kwarai💃💃 Hajiya Fusam na zaune a kasar Niger domin yin magana da ita kai tsaye tuntuɓi wannan number 97 82 44 94 *SECRET DE LA FEMME DU MANGA* Gidan Kamshi, Sirrin Manyan Mata💃💃💃💃💃 Da jin haushi ya ce" Au kin manta wace kika dage sai ta daina saka hijab ko? Wace kika kama hijabinta a filin Allah zaki masa diban albarka wai ki ga kumarinta? Wace kika ringa fadin zantuka mararsa dadi dan ta yi kwaliya maimakun ki mata fada? Bari ki ji, kika yarda Aba ya hadani tafia Haji da ke dama a cen zan maki aure na dawo dan kin isheni!" Daga haka ya mike ya yi gaba yana jin sam bai huce ba in ya tsaya iya haka, kamar wanda bai mata komai ba yake ji, ji yake a cikin ransa ya zama wajibi ya sake wanke babar mai kwanoni ko zata dawo hayacinta ta daina aikata aiyuka mararsa kyau A wannan dare kwata kwata Yumna bata gane kansa ba Irin dan janyota jikinsa da yake yi wani lokacin har ta dan fuskanci yanada bukatarta sosai a wannan daren bata ga haka ba Karshema a dole ta fito ta Bara masa dakinsa dan daure fuskar na hadasa mata faduwar gaba ta zo ta kwana a nata dakin idannuwanta biyu tana hawaye Ba za'a gane irin radadi da tashin hankalin da take tsintar kanta a duk lokacin da ta ga fuskarsa ta cenza ba Ko a lokacin da take da dama irin na budurwarsa ba matarsa ba bata cika iya hadiye ganninsa rai bace ba bale a yanzu da shine mai sarautar ita kuma bafadiya (a ganninki ba) Sosai ta ringa neman mafita a zaune ba a saman salaya ba So take yi ta gane meye a lalle sai ta je ta zauna da kakarsa? Ta ki ta fahimci yarensa bale har ta yiwa tufkar hanci tun ba'a je ko'ina ba, gaba daya ta kasa gane Yaren shima mutun ne mai zuciya a kirjinsa da kuma ahalinsa a cikinta, tashin farkoma bata yiwa kanta shinfida mai kyau ba da take tunanin sonsa ama kuma ta ki danginsa wannan shine wahalarta har kiraye kirayen sallar asubahi ya tasheta daga zaunen da take jiki ba karfi ta saurara ko zata ji ya tasheta kamar yadda ya saba, kanta kuwa ciwo yake kamar zai fashe mata tsabar sakawa kai damuwa A lokacin da ya bude kofarta salama a bakinsa kasa kasa idannuwansu suka shiga junna a lokacin ne ya dan zuba mata ido kadan ya ce" Ki tashi ki yi sallah.........." Da sauri ta riko hannunsa tana mai fashewa da kuka ta ce" ka yi hakuri in na bata maka dan Allah, ba wani abu ya hannani wuni ba ciwon kai mai tsanani nake fama da shi, ka ji? Taba kaina ka ji yanzu haka yadda yake sarawa.....plz ka yi hakuri" Har ga Allah sai ya ji tausayinta sosai ya shiga zuciyarsa A hankali ya taba gaban goshinta sannan ya bita da kallo Yannayinta na masa kama da wace ke dauke da karuwa a matsayinsa na baban likita gane hakan ba zai masa wahala ba bale macen da shine ya santa ya cireta daga sahun budurwa zuwa Mace cikakiya Da kula ya ce" Sorry, ban sani ba ai, ki je ki yi sallah ina zuwa" Da wannan ta samu nutsuwarta ta dawo jikinta, dama a kwanan da ta yi mafitar da ta samarwa kanta kennan, ta san mijinta ba jahili bane, ba kuma wanda baya jin tausayin mace bane, ta tabata zai sauko shi yasa ta sake riƙe damarta har ta isar da sakonta Ko da ta gama sallah a nan ta yi kwonciyarta tana kudurtawa ranta cewa a kan wancen tsohuwar ce har zai iya fushi da ita? Lalle dolema ta tsani matar! Bai wani jima ba ya dawo daga masallacin sannan ya wuce dakinsa ya wuce wajen ajiyarsa ya dauko maganin da ya san koda da wani abin ba zai mata ila ba ya nufi dakinta yana dan duba agogo da tunanin ko abansa ya fito daga masallacin ne, domin cikin dare ya shigo garin basu gana ba Dakin ya shiga, cikin kula ya bata maganin da kansa sannan ya sakata fitowa dan ta ci wani abin A lokacin da suka dan fara karyawa kiran Aba ya same shi a wayarsa cewar ya same shi bangarensa Gamawa ya yi da dan gaggawa ya mike ya tafi sanye da jalabiya maroon mai haske kafarta da takalmi plate baki sai dan carbin dake hannunsa yana tafe yana shaƙar sansanyar iskar safiya har ya karasa bangaren Mai kwanoni Tunda ya bude falon ya gansu su duka zaune , watau matan Elhajin da Elhajin da kuma Hajia a zaune ta yi wani dauri gayanan dai kamar jirgi a saman kai hijab din ya tafi tsakiyar kanta sai wani MUSMUS take da baki ya ayana' To fa, na yi wani abin kau?' Karasawa ya yi ya shiga gaisar da iyayensa bayan ya gaishe da Abansa cikin mutuntawa kamar yadda ya saba Yana gamawa Aba ya ce" Kai, dan matso daga nan ka turaru, kai yanzu tsakani da Allah magidanci turaran tsarin ne ka dauki kwana uku cir baka yi ba? Kuma ka saka min uwata a gaba ka wanketa tasss?, Ta maka kyau, nace ta maka kyau sai ka matso ka turaru sosai ka kuma dage rigar ta shafa maka na shafawar idan kuwa baka yarda ba to ka sanar min na ji" Murmushi kawai mahaifiyarsa ke yi kanta a kasa, tana matukar mamakin irin soyyayar da Hajia ke yiwa TAUFEEK, a kashedin da ta kawo har tana haki Elhaji ya kwashi ya fada yana fadin lalle yau zai sasabawa TAUFEEK din, sai cewa ta yi ita bata fada dan a masa fadace fadace ba, ta fada ne dan a saka shi ya zauna ta masa turare turarensa...., Watau irin yadda Hajia ke saka TAUFEEK a gaba ko Elhajin bata cika damuwa da ya yi turare tutarenta ba Hajia harda sauke ajiyar zuciya ta saki murmushi ta ce" Dawo daga nan magidanci, ku kuwa ku tashi ku dan bamu wuri ai ba a gabanku zan masa shafen danyen man ba ko?" Matansa dama sun san da su ake, a zaunen da suke kowace tamkar zata fashe dan jin haushi, ita dayar har ji ta yi alamun nakuda na tsikararta dan bacin rai, su dai har ga Allah matar nan da jikanta da kishiyarsu sun gama tsaye masu a wuya, ta yaya za'a ce mijinsu ya zo sun zo a zauna a yi fira ya ji yaya ya bar iyalinsa ama ta zo ta yi bake bake? Shi jikan nata ai yana da hankali domin da shine dan radin kansa ba zaka ganshi nan ba har sai uban ya kirayeshi, duda shima uban baya iya zama sai yana kiransa bini bini ka ga ya daga waya yana tambayar yana ina ne Baki ta tabe a ranta tana ayana' in dai namiji ne? Ina ji a jikina nima shine a cikina, zan haifo shi na ga tsiya nan kusa ba da jimawa ba!' Abinda ya birge Aba , Hajia na fadin su tashi harda Mama ta mike itama ta bi yan uwanta, irin karar nan da take yi idan mahaifiyarsa na wasu abubuwan na saka shi jin nutsuwa a zuciyarsa, domin har ga Allah wani abin ya san bai dace ba sai su ga dan ba su suka haifa ba, ama in ya ga Mahaifiyar TAUFEEK ta shige ayarin sauran sai ya samu kansa da sakin murmushi, watau matar nan itace ake kira matar rufin asiri mai kwontar da hankalin mai gida, ya tabata kuma suma zasu ji sanyin a ransu in suka ga fadan na Hajia ba iya su ya tsaya ba harda uwar TAUFEEK din Duka kaf abinda ya dace ta masa ta masa sai sakin murmushi take tana masa magana kasa kasa tana aukin fadin" Allah ya baka hakuri ka ji magidanci? Ni na san koma waye ya taba min kai ba da gangan ya yi ba, khausara ai ba halinta bane bale nace itace ko? To koma waye ya je dan kansa Ni ba zai rikita min kai ba ka ji? Gama ganawa da MAHAIFINKA ka zo na dama maka fura da kindirmo haka take laudi ka sha abinka ka ji?" Shi dai bai ce mata komai ba har ta dauke kaskonta ta yi gaba, dama abinda ya dameta kennan ta kuma yi, sauran rikicin a yi mana sai me Tana tafiya Aba ya sauke murmushi a bayane yana duban TAUFEEK dake gaishe shi da yi masa Barka da zuwa gida lafiya Bai bi ta kan gaisuwar ba ya ce" Yanzu ɗan mai Kwanoni uwata zaka yiwa aure a Saudiya???" Shima abin sai ya bashi dariya har ya murmusa sosai yana murza gaban goshinsa Elhaji ya sauke ajiyar zuciya da kula ya ce" Kai da waye wai? Nake gannin fara'arka du ta ragu?" TAUFEEK ya dago dubansa ya zubawa mahaifinsa shi A hankali ya sauke ajiyar zuciya yana Basar da zancen a harshensa ya ce" Ba komai Aba, shirmen Khausar ne kawai, ta gama service dinta a hospital din nan sai nace a kaita clinik, docteur bai fahimci tashi nake nufi ba sai kawai ya turata Lafiya, kuma a ranar ina gabatar da aikin nan na binciken ma'aikatana.....shine inaga abin ya bata mata rai sosai wai ko na boye mata, harda su cewa zumuncina da ita ba gaskiya bane ta soke komai........" Ya karashe maganar yana dan girgiza kansa da dan fitar da wani murmushi mai ciwo wanda kana gani zaka gane ba murmushin bane ya yi na kirki, a'a irin murmushin nan ne mai zafin nan Kallonsa mahaifinsa yake yi, kallo irin mai tarin ma'anonin nan A hankali ya sauke ajiyar zuciya yana sake duban ɗan nasa......... , Yakan tambayi kansa shin yaron nasa tsabar nauyin baki ne ke hadasa masa wannan abin ko kin gane gaskiya ne? Shin me yasa yake nan yana jira yana sakawa kansa ciwo a banza da wofi? A hankali ya ce" kana nufin a yadda kuka shaku, shekara ta hudu zuwa biyar, baka kwatanta mata wanene kai ba MAGIDANCI?" A hankali ya dan zubawa fuskar mahaifinsa ido, sai yake tunanin kamar shima ganni zai yi bai kyauta ba? Ko menene? Ajiyar zuciya mahaifin nasa ya sake saukewa yana dan juyar da dubansa ya rage sanyin acn dake busawa Da kula sosai ya gyara zamansa yana fuskantarsa ya ce" ka gane, In shekarun ka ajiye hudu nema ka jima da kaiwa , in halin kula da bukatunsu ne inaga kana iya rike wani gidanma ba naka ba, ko lafiyarka ne ba zata baka damar ajiyeta a gefenka ba? Ko ...........," Ya dan sasauta ya sake dubansa gannin ya yi wani tsuru yana kallonsa ya karasa maganarsa kai tsaye tunda dai shi din ai shine mai kwanoni uba a wajensa ba zai batar da shi a Saudiya ba ko?, A nutse ya ce" Ko tsoro take baka yannayinta ne?""" Da sauri ya cire dubansa daga kan mahaifinsa, wani irin abu na masa yawo a kwakwaluwa da zuciya A nutse ya juyo yana fuskantar mahaifin nasa kamar yadda shima yake fuskantarsa , Da darajantawa irin ta d'a da mahaifi ya ce" Aba, Ni du ban gane abinda kake nufi ba, wace? Mene? Yaya?" Murmushi mahaifin nasa ya yi bayan ya masa kallon ba dai zaka daina musawa ba ko?, Sai kuma ya dauke dubansa a hankali ya juyar wajen takardar dake gefensa ya dauko ya mika masa ya ce" Na jima da fada maka, ba fa zan ci gaba da saka hannu a harkar gidajen da ake haya ba, TAUFEEK its time da zaka tsaya ka zauna ka ga me zai fisheka, dan ka ga Ni Na fa ajiye kuma, kasuwa dai zan ci gaba da zuwa ko dan mutanena in ringa cenza yannayina nima ina jin dadi, ama du wasu kofofin dake kawo kudi na miko maka, kaine baba, kaine ya dace zuwa yanzu ka amshi komai dan Ni na gaji , kai in ba dan ban fara gannin yan jikokina ba ai da na jima da mayar da falon nan filin ball, ka je ka duba ka daidaita lamuranka na san ba zaka taba ajiye aikinka ba, sai dai kuma ka sani Ni ba iyayenka zan ba aikin nan ba, naka ne ka dai daidaita kanka kawai" A hankali ya ninke takardun stil yana dan satar kallon mahaifinsa, sai dai kawar da zancen da ya yi shima ya fi masa alkhairi domin bai san me zancen ke nufi ba........ 🥹🥹🤔🤔🤔🤔🤔🥹🥹🥹🥹🥹 💔💔💔💔❤‍🩹❤‍🩹💔💔💔💔 *DA CIWO A ZUCIYATA* 💔💔💔💔❤‍🩹❤‍🩹💔💔💔💔 _MALLAKIN_ *SAJIDA NIJAR* *FREE BOOK NE* 3️⃣2️⃣ *GARABASA, GARABASA, PROMOTION, PROMOTION DIN LITATAFAN MARUBUCIYAR A KAN FARASHI MAI SAUKI 1K, YAN NIJAR KUWA 1000 FRANCS CEFA* 1: Duk karyar kada 2: Yar mahaukaciya 3: Neman na kaina 4: Bani da zabi 5: Bak'a ce 6: Kutkale 7: Makauniya ce 8: Mage 9: Duk nisan jifa 10: Idan ka raina inda kake 11: Dutse 12: Alkalamin kadarata 13: Bani da zabi 14: Dakika Biyar 15:Wata kokowar 16: Aure yakin mata 17: Ni zan ladabi 18: Daga tafia daukar soja *Dukansu a kan farashi mai sauki, zaka saka dubu guda ne domin promotion ne nake yi, ka tuntubeni kan layina kamar haka +227 93 81 16 18, Sajida Nijar* Now *Da CIWO A ZUCIYATA* *Tallah, tallah, tallah* *SECRET DE LA FEMME DU MANGA* _Gidan Kamshi, Sirrin Manyan Mata, nesa tazo kusa,Amarya ,Uwar gida,Ango da mai gida Har ma da yan mata da samari shin kuna sane da cewa HAJIYA FUSAM ta shirya tsaf domin gwangwaje ku da turarakunta masu dankaran kamshi? Tare Kayan gyaram jiki na musamman ,wanda daga nesa kamshin ki kadai ya wadatar ya isar da sakon zuwanki waje,gidan ki kuwa sai ya zam abun kwatance wajen kamshi, kar na cika ku da surutu bara in fara zayyano su_ Farar Humura Bakar Humura Humura special, humura de bain Humura epicé Lait de nuit Parfums désodorisant Parfums rideau et dras Lait de nuit Alkam Kulakcam *Waɗannan kadan ne daga bangaren turaran ruwa* Gagab, sandal flex, Durot, durus, sandal fleur, tafarce, farce, sandal bangui, sandal, hypotonic sandal, al'ut, coktail creation VIP, Gajiji, Mankaji, turaran wutar labule da cafet, Aba malan, boulettes *Munada bangaren gyaran jiki kamar haka:* mai mai saka santsin jiki, mai mai kanshi, Kayan gyaran jiki mai saka fata ta yi santsi da laushi, kayan gyaran jiki mai saka fata ta yi fari, Sabulu mai saka fata ta yi haske, sabulu mai saka fata ta yi santsi, sabulu mai goge yanayin fata, mai wanda baya saka fari mai gyara fata Sayen na gari mai da kudi gida,sai an gwada akan san na kwarai💃💃 Hajiya Fusam na zaune a kasar Niger domin yin magana da ita kai tsaye tuntuɓi wannan number 97 82 44 94 *SECRET DE LA FEMME DU MANGA* Gidan Kamshi, Sirrin Manyan Mata💃💃💃💃💃 Ya dan jima zaune sunna dan tataunawa kafin ya mike gannin har tara ta gota kuma ga ayyukan dake gabansa ya juya yana kokarin tafia Elhaji ya kirayi sunnansa yana kallonsa Juyowa ya yi dan kiran yana masa ya shiga magana Da kula ya ce" Shi rike kashi a ciki bashi da wani anfani, Ni kuwa nan da ka ganni bana tunanin in zan iya hakurin jure kallonka a wani yannayi na tsayin lokaci, idan har baka yi kokarin ganin ka samawa kanka mafita ba nine nan zan sama maka ita da yardar Ubangiji, ka ji da rigingimmunma ya isheka ba sai ya hadu da rikicin zuciya ba, mu wuni lafiya" Tsakani da Allah a yadda ya zubawa abansa ido , ido rufe so yake ya gane inda ya dosa, sai dai sam bai bashi damar haka ba ya sake daure fuska ya cire kai daga dubansa , a dole ya fice yana ta tunanin me magangannun nan ke nufi? Fadanma da ya yi tunanin zai masa bai masa ba sai wasu yare gasunnan dai...., Ajiyar zuciya ya sauke kawai ya ci gaba da HULDODIN gabansa , a dole ranar bai je asibiti ba dan abubuwa sun masa yawa wuni ya yi yana aikin dukiyar mahaifinsa har yama ta yi sannan ya sake yin wanka ya saka sasaukan yadi mai ruwan madara tassss ya fito a nutse ya nufi Masallacin anguwar Bayan an fito daga sallah ya samu kansa da sake gwada layinta, still dai yana a rufe...., Wani abu mai zafi ya tsaye masa a wuya, dan haka rai bace ya nufi ciki ya karasa bangaren Hajia dake turara turaran jiji a filin gidanta ya dogane da yannayin nan nasa mai kamewa sosai da tsari a lafuzansa ya ce" Dauko hijab dinki ki rakani" Hajia ta dan zuba masa ido ta shiga duniyar tunani, ina suka nufa to? Sai dai tunawa da ta yi da ai mai kwanoni na gari ta je ta dauko hijabinta dogo irin wanda yake so tana sakawa ta zumbula ta shafa turarenta dan dure sannan ta dauko carbinta da wayarta ta fito ta karasa wajen motarsa ta bude ta shiga tana sakin murmushi ta ce" Ina muka yi magidanci ko gidan zoo?" Bakin nata da ta ambaci zoo din ya kalla ya cire kai a ransa ya ayana' ai kecema zoo din , da daren nan dan mune aljannu zamu je gidan zoo mu yi me' A bayane kuwa sai ya girgiza kai bai ce mata komai ba ya ringa tukinsa hankali kwonce har suka karaso anguwar Baki Hajia ta washe ta kalle shi ta ce" Sai kace wajen Khausara zaka kawo Ni mu yi zumunci, Allah sarki Khausara yarinyar kirki shiru shiru abinta bata cewa komai, Allah ya nunan aurenta na tsumata na tsumumuwata na maka mata magungunan nan na yaran mata ta jiku iya jikuwa ta ringa zubar da........." "Idan baki yi shiru ba kin san Allah zan sauke ki a tsakiyar titin nan na yi tafiyata, ke wai bakinki baya fadin magana mai dadi sai magangannu irin na gasunnan dai? Ki fa kiyayeni in ba haka ba ina kan bakana sai mun shige cikin samudawan nan na bace maki su dauka su tafi da ke kowama ya huta!" Ya fada a zafafe bayan ya taka birkin motar Tsitttt Hajia ta yi tana kale kale, idan ba gizo gizo Bama idannuwanta ke maga a gefen cen ai taron samari ne bata gari da karnukansu, yanzu idan ya zubar da ita a nan ai shikenan ya tonawa mai kwanoni asiri, gwara ta yi shiru su je su dawo ita kam yau mai rabata da shi sai Allah A nutse ya karasa kofar gidan ya tsayar da motar sannan ya sake fuskantar ta Yanzun a tausashe kadan ya budi bakinsa ya sanar mata ainahin dalilin da ya da ya daukotama ya zo nan din da ita Kallon da take masa kamar wani wanda ya aikata sabo Da kyar ta iya budar baki bayan ta tabe ta wani cira kai ta ce" To da bata yi haka Bama sai na san yadda na yi da ita, da kai macuci ne Magidanci? Yanzu Khausararma ka cuta to waye zaka bari? Innalilahi wa inna ilaihi raj'une, dole ya ta gigice ta fita hayacinta, ka ce yanzun ba makiyinta sama da kai kawai?" Kansa ya mayar ya jingina da kujerar ya lumshe manyan idannuwansa a hankali ya hadiye sawun dake makogwaronsa ya shiga tunanin anya ba ya tafka kuskure da ya zo da matar nan ba kuwa? Yanzun fa ya fada mata yana so ne kawai ta yiwa yarinyar cen fada komai ya wuce, ama ji abinda bakinta ke fada "Kai, lah, buda ido kalli ikon Allah kamar khausara da kato?" Hajia ta fada tana jimko hannun TAUFEEK Tsakani da Allah wani irin sarawa da kansa ya yi lokaci daya hadi da wani irin kamewa da kirjinsa ya yi masa bai san lokacin da ya bude idannuwansa ya zuba su a inda Hajia ta nuna masa Lokaci daya ya sake zuba idannuwan nasa har Hajia ta fice bai sani ba Yana nan zaune yana kallon dukawar da Khausar ta yi ta gaisar da Hajia da kuma shima wanda suke taren rage tsayinsa da ya yi yana sosa kai da abin ky din hannunsa yana ta sisine kai Hajia kuwa na magana har dai saurayin ya fice ya tafi sannan suka shige ciki ita da Khausar shi dai yana zaune idannuwansa a kafe a dokin kofar gidan Bai san irin lokacin da Hajiar ta dauka a ciki ba, bai san me da me ta tafka masa ba, yana nan zaune a motar Ac na yi dan motar a kunne take Har Hajia ta fito Mama na biye da ita, KHausar kuwa dauke da kwano rufe ta karaso wajen motar gabanta na faduwa kanta a kasa ta bude bayan motar ta ajiye kwanon saman kujera a hankali ta dago dubanta ta saci kallon gaban, ai kam idannuwansu suka shige cikin junna, nata idannuwan da abin hawaye hawaye, nasa kuwa sun yi wani irin jajajir din da bata taɓa ganninsu a haka ba sannan yana mata wani irin kallon da zata iya fasara shi kamar wanda ke jin haushinta , dan haka a hankali ta sinne kanta ta ja numfashi sannan ta rufe motar ta dawo ta shige gida bayan ta yiwa Hajia salama, Mama kuwa da Hajia a nanma sun dauki sama da minti biyar sunna zantawa kafin Hajia ta karaso ta bude tana kallon TAUFEEK ya gaisar da Mama muryarsa a cakude, maman ta dube shi da kula ta ce" Ashe shiriritar da yarinyar cen ta tafka ko? Ai zata hadu da Ni ne, ana katse zumunci ne dan kawai iya shege? Ka yi hakuri ka ji, in sha Allah zama ta nemeka ne ta baka hakuri!" Shi dai bakinsa gaba daya ya masa wani irin nauyin da bai san dalili ba Yana kallon Hajia ta dauko kwanon ta rungume a gabanta ta ce" Ka ga rashin sannin darajar koko, a baya ta dingile shi salon Ya zube na yi asara?, Ja mu je na bada maka maganin mugun ci ka sha ka raga min na sha nima" Mama kam tana murmushi tana kallo ya tashi motar suka tafi sannan ta koma gidan Ranta bace ta karasa dakin Khausar ta nemi waje ta zauna ta ce" ............ku taimaka ku yiwa sajidale solidarity😌😌, ga promotion din, sai na ji ku😔😔😔😔 *GARABASA, GARABASA, PROMOTION, PROMOTION DIN LITATAFAN MARUBUCIYAR A KAN FARASHI MAI SAUKI 1K, YAN NIJAR KUWA 1000 FRANCS CEFA* 1: Duk karyar kada 2: Yar mahaukaciya 3: Neman na kaina 4: Bani da zabi 5: Bak'a ce 6: Kutkale 7: Makauniya ce 8: Mage 9: Duk nisan jifa 10: Idan ka raina inda kake 11: Dutse 12: Alkalamin kadarata 13: Bani da zabi 14: Dakika Biyar 15:Wata kokowar 16: Aure yakin mata 17: Ni zan ladabi 18: Daga tafia daukar soja *Dukansu a kan farashi mai sauki, zaka saka dubu guda ne domin promotion ne nake yi, ka tuntubeni kan layina kamar haka +227 93 81 16 18, Sajida Nijar* 💔💔💔💔❤‍🩹❤‍🩹💔💔💔💔 *DA CIWO A ZUCIYATA* 💔💔💔💔❤‍🩹❤‍🩹💔💔💔💔 _MALLAKIN_ *SAJIDA NIJAR* *FREE BOOK NE* 3️⃣3️⃣ *GARABASA, GARABASA, PROMOTION, PROMOTION DIN LITATAFAN MARUBUCIYAR A KAN FARASHI MAI SAUKI 1K, YAN NIJAR KUWA 1000 FRANCS CEFA* 1: Duk karyar kada 2: Yar mahaukaciya 3: Neman na kaina 4: Bani da zabi 5: Bak'a ce 6: Kutkale 7: Makauniya ce 8: Mage 9: Duk nisan jifa 10: Idan ka raina inda kake 11: Dutse 12: Alkalamin kadarata 13: Bani da zabi 14: Dakika Biyar 15:Wata kokowar 16: Aure yakin mata 17: Ni zan ladabi 18: Daga tafia daukar soja *Dukansu a kan farashi mai sauki, zaka saka dubu guda ne domin promotion ne nake yi, ka tuntubeni kan layina kamar haka +227 93 81 16 18, Sajida Nijar* Now *Da CIWO A ZUCIYATA* *Tallah, tallah, tallah* *SECRET DE LA FEMME DU MANGA* _Gidan Kamshi, Sirrin Manyan Mata, nesa tazo kusa,Amarya ,Uwar gida,Ango da mai gida Har ma da yan mata da samari shin kuna sane da cewa HAJIYA FUSAM ta shirya tsaf domin gwangwaje ku da turarakunta masu dankaran kamshi? Tare Kayan gyaram jiki na musamman ,wanda daga nesa kamshin ki kadai ya wadatar ya isar da sakon zuwanki waje,gidan ki kuwa sai ya zam abun kwatance wajen kamshi, kar na cika ku da surutu bara in fara zayyano su_ Farar Humura Bakar Humura Humura special, humura de bain Humura epicé Lait de nuit Parfums désodorisant Parfums rideau et dras Lait de nuit Alkam Kulakcam *Waɗannan kadan ne daga bangaren turaran ruwa* Gagab, sandal flex, Durot, durus, sandal fleur, tafarce, farce, sandal bangui, sandal, hypotonic sandal, al'ut, coktail creation VIP, Gajiji, Mankaji, turaran wutar labule da cafet, Aba malan, boulettes *Munada bangaren gyaran jiki kamar haka:* mai mai saka santsin jiki, mai mai kanshi, Kayan gyaran jiki mai saka fata ta yi santsi da laushi, kayan gyaran jiki mai saka fata ta yi fari, Sabulu mai saka fata ta yi haske, sabulu mai saka fata ta yi santsi, sabulu mai goge yanayin fata, mai wanda baya saka fari mai gyara fata Sayen na gari mai da kudi gida,sai an gwada akan san na kwarai💃💃 Hajiya Fusam na zaune a kasar Niger domin yin magana da ita kai tsaye tuntuɓi wannan number 97 82 44 94 *SECRET DE LA FEMME DU MANGA* Gidan Kamshi, Sirrin Manyan Mata💃💃💃💃💃 Ranta bace ta karasa dakin Khausar din ta dage labulen ta shiga ta zauna lokaci daya Khausar ta dago kanta daga dukewar da ta masa tana kallon Mama lokaci daya mama ta ce" akoy wani abu tsakaninki da TAUFEEK ne bayan zumunci da ya danganci soyaya ko makamancin ta?" Da sauri Khausar ta kallo Mama tana zarro ido, lokaci daya ta girgiza kai ta ce" Kai , astagfrullah mama da Taufeek kuma?" Mama ta dubeta da mamakin itama jin astagfarin da ta yi, sai kuma ta tabe baki ta ce" To me kennan? Me Hajia ke fadi haka? Ki karra daure masa fuska sosai ko me?, Bani haske mana na ji?" Khausar ta sake lumshe idannuwanta wasu hawayen suka biyo su, a raunane ta ce" Mama, wai du tsakanina da TAUFEEK ace yana boye min wasu sirikansa? Yaya yake so na dubi alakarmu kennan? Ni na zata zumunci muke yi na gaskiya wanda ba karya a ciki, sai kawai na kama shi da wannan baban abin? Mama ya zamo min kamar wani bako, kar ki so ki ga yadda ake girmamashi a wajen aikin nan, baba da yaro, ashe shi din baban likita ne muke zaune ya rufeni? Mama ki duba ki gani menene bai sani ba nawa? Ni me nake boye masa ne?, Ni kam ba zan iya ci gaba da wani zumuncin da shi ba, dan na gama dauka cewar kallon shashasha yake min wace ban san ciwon kaina ba, in ba wannan ba a shekarun nan ai da ya kamanta sanar min wanene shi, Mama asibitin lafiya fa shine mai ita, baban likita ne har muƙamin inspector gareshi, me kennan? Mutumen da nake tunanin na fi kowa sanninsa sai na ga nice ban san waye shi ba? Me kuma ya rage?, Ai ya gama bankadar min da komai ko Mama?" Ta karashe tana jin ciwon abin nan har cikin ranta, Mama ta sauke ajiyar zuciya tana kawar da tunanin da ya darsu a ranta ta zauna da kyau tana fuskantarta ta ce" shine zaki yi fushi har haka?, Aikinsa ne fa ya zo masa a haka, bayan wannan din akoy wani abin da kike gannin bai kyauta maki ba da ya taba aikata maki?, Khausar sai nake gannin kin dauki abin nan da zafi, ke da kanki kin san a duniya yana mutuntaki ko? KHAUSAR a tunanina abin alfaharine, kina kallo ba dangin iya ba na Aba yake zumunci da ke, ke kadarama dan ya gane mutanen da basa maida hankali a makarantarku ne din ai ina ganin a kan dalili mai kyau yake tsaye ko?, Ke dinma kina da ladan hakan ko menene?, Khausar ki duba ki gani kina gama karatu kin shige babbar asibiti kin koyi aiki cikin jin dadi dan ke ake koyawa kuma ake ba albashi, kina gamawa gaki yau kece likita a asibitin nan wace da muna firar da wata bakuwar maman biyu sai da ta sake kallona tace lalle mun yi Sa'a, tana son numbarki dan in zata je ta ringa kiranki wai ai asibitin ka samu shigama sai ka dace da Sa'a? Haba Khausar, ke da zaki yi murna ki yi farin ciki ki taya shi da addu'a? TAUFEEK ne fa, yau kuma har ake jin kanku? Ai saima ya ga bakya farin ciki da kasantuwarsa haka ko? Ko kin fi ya kasance maki dai wannan mai shiriritar abokin naki da bai samu gama makaranta ba?, Haba yar gidan Aba ke da kanki??????" Khausar ta sake sinne kanta ta gaza ba Mahaifiyarta amsa, zuciyyarta na tsintsinkewa tana jin kamar bata kyauta ba, tana kuma jin ai shine bai kyauta mata ba tunda yana tunanin ba zata iya rike sirinsa ba haka Mama ta bata lokaci tana mata nasiha kan lamarin, har ta umarceta kan ta je ta bashi hakuri goben ta mayar da komai ba komai ba, su ci gaba da zumuncinsu har a ga yadda Allah ya yi, sannan suka tatauna kan bakon nan nata na yau, bako daga zuwa da maganar aure? Eh lalle an sanshi shi din mai sauki ne kan halayan yan gidansu, sai dai ai ba shi zai aurar da kansa na, harda cewa a yau sai ya hadu da Aba ya gaishe shi ya nuna masa yana so? Lalle ko bai zo da wasa ba da gasken yana so din, ko kuwa wani kasurgumin dan rainin hankali ne, wai tafiya zai yi yana so kafin ya tafi a daura masu aure sai ya tafi ya dawo? A nufinsa tafiyar ba zai jima ba zai yi ta?, Lalle yana tare da baban lamari, ta yiwu kuma ADU'ARSU ce Allah ya amsa tashi daya ya kawo mijin ashe a kusa ma yake, kuma gashi ba za'a bata lokaci ba? Kai kuwa da sun ji dadinsu su kam, dan haka yanzunma aduar ta yi a kan lamarin sannan ta fice tana jiran Aban Khausar din Sosai ta KWONTA da abin a ranta, abubuwa biyun nan, damuwar TAUFEEK sai kuma maganar bakonta, eh lalle bashi da laifi kuma kai tsaye da Mama ya zanta, a maganar nasihar mama kuwa kwarai ta shige ta, ama har yanzu tana jin haushin abin bata san dalili ba sai dai abu daya ta san zata iya aikatawa shine bin umarnin na Mama, zata je ta bashi hakurin ne , ama a cen kasan zuciyarta bata ji in har zata iya dawo da zumuncinsu irin na da ba A bangarensa kuwa, a wannan dare Yumnah ta amshi maza iya maza, har sai da ta fara sarewa duniya domin bata taba tunanin bayan azabar da ta sha ta first night karatun na jiranta ba, dan kamar wanda wani ya kunno shi, ko shi din kansa cikin Sannin kansa yake? Abinda ya sani zuwa biyu rak da ya mata ba asalin shine abinda ya sa ya amayar da damuwarsa ba, dan ji yake yi kamar ya dan shafa bayan kwarya ne, sai dai gannin irin jigatar da ta yi sai ya daga mata kafa ya bata lafiya, ama ina tsabar ta wahala jikinta ya ki amsa tun karfe bakwai na safe ya gama kimtsawa sannan ya taimaka mata ya shigar da ita mota hankali kwonce ya nufi asibiti da ita, baya wani Dari dari, hasalima yana so ya ga ita din idan ta san waye shi me zata yi dan kuwa a kasan zuciyarsa ya gama yarda cewa a nan zai nunawa mata yana da zuciya shima a jikinsa! Karfe goma Khausar ta nufi hawa matatakalar office dinsa kanta tsaye Eh lalle ta ringa jin wani abu mai kama da shayi a zuciyyarta bale idan tana karra kusanta kanta da office din tana sake gannin girmansa a bayyane , sai dai wani gefe na zuciyyarta ke fada mata *TAUFEEK NE, BESTY DINTA* ko me ya zama shi dinta ne dai, da izinin ubangiji ta san zasu sasanta a wuce wajen fushin Da nutsuwa ta kama abin budewar ta bude bayan ta dan buga , bakinta dauke da salama kasa kasa tana wara dubanta dan son hango shi A hankali idannuwansu suka shige cikin na junna, Yumnah dake kwonce saman doguwar kujera idannuwanta lumshe tana aukin tunanin abinda ya tsaye mata a zuciya ta rasa mai bata amsa tun zuwansu asibitin nan da mijinta da irin gaisuwar da ake masa ana sir sir, da office din nan da suka shigo, yana shirye shiryen duba lafiyarta wanda hakan ya matukar bata mamaki duba da ai bai gama karatunsa ba, sai baban mamakin ya risketa wani likita ya shigo da wani file suka duba tare cikin dan gaggawa TAUFEEK nata ya shige cikin dakin cen, jim kadan sai gashi ya fito cikin shiga irin ta likita, likitanma baban Likita a gaban rigar da siririn rubutu an rubuta DOCTER TAUFEEK, wanda hakan ya kusan sumar da ita, har ya tabbatar mata yana zuwa zai je tiyatar gaggawa ya dawo ne, yanzu abin ya same shi, ya fice kusan awa biyu da rabi kennan tana kwoncen nan zuciyyarta ta gama cicira mata lisafi sai yi take ta rasa me zata fahimta dan abin nan ya zo mata a ba zata, tarin tambayoyin dake kwakwaluwarta kuwa tamkar zasu fasa mata kai ne, sai ta matar da ta jima bata gani ba , wato mayar mijinta ta shigo da shigar itama irin na likitocin, harma shigarta ta so tsoratata domin sket da riga ne na atampa masu ruwan blu a ciki sai riga fara dake saman su sai dan karamin mayafi sosai da ta dan yane kanta da shi , hannunta daya da agogo dayan ba komai , wuyanta da abin awo irin na likitoci, kaffafuwanta sanye da takalmi plate mai masifar kyau dan ya dauki yan kaffafuwanta da basu da girma, idannuwanta da kwali radau lebenta kuwa da dan jan baki madaidaici uwa uba kanshin da ta shigo da shi kanshi ne mai sanyi du irin kanshin da office din ke yi kuwa ana jin nata kanshi ne mai sanyin gaske da kuma nacin waje, sai kawai Yumnah ta zama mutun mutumi ta zubawa Khausar din ido ta kasa amsa koda gaisuwarta dan sai ta fara tsoron ko ba a duniyar mutane take ba yau? Domin wannan da take gani mace ce mai cikakken classs da kanshi bayan wace ta sani tamkar guzumar mace idan tana tafe take? Bakinta ta dan dantse a hankali cike da takaicin sabon rashin mutuncin nan na Yumnah, tana kallonta ta yi salama ai ko salamar ce ta amsa ama sai ta wani kafeta da duba irin na rainin nan ba zata yi mata magana ba? Cire kanta ta yi daga kanta ita dinma, dan kuwa ba zata yarda karamar yarinya ta nemi raina mata wayo ba, a tunaninta rukayama ta girmi Yumnah bale A'isha har a gangaro kanta, idanma wani abu na mata hayaki a kai ta nemi sa'anta ta yi da shi ba wai ita KHausar ba Gannin kamar baya office din ta juyo a Nutsenta zata bar office din, nan Yumnah ta zubawa bayanta ido, domin ƙarara rigar likitocin ta dage saboda uban Bombon din dake bayanta wanda ya yi wani irin yanayi na heart ya yi dasss a jikinta yake kuma juyawa dan radin kansa ba tare da an saka son juyashi a rai ba , domin da aka so juya shi dan neman fitina da lalle an barawa mata abin duba na gani na fada a idannuwansu! Handle din ta kama ta bude dan tafiyarta, a hankali idannuwanta suka sauka a saman fafadan kirjinsa wanda ke cikin riga mai dogon hannu baka sidik mai botura a gabanta hannun rigar daya a tatare har cen saman dantsensa hakan ya bayanar da girman hannun da yannayin karfi ya nuna kansa da irin jijiyoyin nan na kakarfan maza sai byro dake cikin hannun , dayan hannun kuwa rike da wani file ga dukkan alamu magana yake yi ta katse a lokacin da suka yi ido hudu da Khausar din A hankali ya dauke dubansa daga saman fuskarta, itama a hankali ta ja baya ta basu hanya suka shigo domin bayanshi akoy docter biyu, dayar na rike da rigarsa ne , dayan kuwa baya rike da komai sunna ta zantawa ta yiwu kan aikin da suka gama yanzun ne Kanta sade da girmamawa ta gaishe su a jimlace a matsayinsu na iyayen gidanta sannan ta juya a hankali da nufin barin office din , dan ta ga aiki ne suke yi gashima ya nuna kamar bai wani santa ba???? "Nurse...,......." Muryarsa ta katse mata hanzari, wata murya daban da wace ta sani, murya mai cike da isa da iza da kamala, murya mai cike da aji da hobasa A hankali ta dakata, sannan ta juyo garesu, dan a wajen nan dai karamin kwarin idan tana da kwakwaluwa itace, dan haka ta dawo a Nutse ta dakata da ladabi ta ce" Yes Sir" Bai bi ta kanta ba, saman kujerar nan ya karasa ya zauna yana dan wara hannayensa kadan , ya kai dubansa wajen doctor dake gaishe da Yumnah, ita kuwa ta wani gyara zama ta kile abinta tana amsawa cike da aji, dan zuwa yanzu tana daf da gane mijin nan nata fa kamar mataimakin oga ne a wajen nan ko yana kusa da mataimakin ogan Sai da ya gama shan kanshinsa a jimlace ya miko mata katinsa, katin dake iya bata damar zuwa du inda take so a cikin asibitin kanta tsaye idan ta nuna , take kuma da hop din taba du abinda take so kanta tsaye, cike da basarwa ya ce" ki je cafetariat ki sama mana abinci" Katin ta amsa, a hankali ta dan sake zuba masa ido, sai ta ga gaba daya duba ko na second daya TAUFEEK bai yi mata ba A hankali ta juya jiki ba karfi zata tafi ta ji Muryar docter nan macen tana fadin" Sir sai na je na samo abincin mana, kawo katin , Nurse wacece sunnan ki?" KHausar ta dakata ta juyo yanzunma jikin ba wani kwari ta ce" KHAUSAR " Likitar ta karaso da nufin amsar katin, dan a ganninta wannan nurse din ta jiya jiyan nan bakuwa ina ita ina samun darajar zuwa aikensa uwa uba harda katinsa? Ina ba zai yiwu ba, sai dai bai bata damar hakan ba da wannan bakon yannayin nasa ya tare mata hanzari ya ce" A'a, ki barta ta je" ya ci gaba da duba takardunsu hankali kwonce ya yi watsi da su su dukansu! Watsi da su mana, daga maganar nan TAUFEEK bai sake cewa da su uffan ba har Khausar ta juya ta fice tamkar an zare mata laka 💔💔💔💔❤‍🩹❤‍🩹💔💔💔💔 *DA CIWO A ZUCIYATA* 💔💔💔💔❤‍🩹❤‍🩹💔💔💔💔 _MALLAKIN_ *SAJIDA NIJAR* *FREE BOOK NE* 3️⃣4️⃣ *GARABASA, GARABASA, PROMOTION, PROMOTION DIN LITATAFAN MARUBUCIYAR A KAN FARASHI MAI SAUKI 1K, YAN NIJAR KUWA 1000 FRANCS CEFA* 1: Duk karyar kada 2: Yar mahaukaciya 3: Neman na kaina 4: Bani da zabi 5: Bak'a ce 6: Kutkale 7: Makauniya ce 8: Mage 9: Duk nisan jifa 10: Idan ka raina inda kake 11: Dutse 12: Alkalamin kadarata 13: Bani da zabi 14: Dakika Biyar 15:Wata kokowar 16: Aure yakin mata 17: Ni zan ladabi 18: Daga tafia daukar soja *Dukansu a kan farashi mai sauki, zaka saka dubu guda ne domin promotion ne nake yi, ka tuntubeni kan layina kamar haka +227 93 81 16 18, Sajida Nijar* Now *Da CIWO A ZUCIYATA* *Tallah, tallah, tallah* *SECRET DE LA FEMME DU MANGA* _Gidan Kamshi, Sirrin Manyan Mata, nesa tazo kusa,Amarya ,Uwar gida,Ango da mai gida Har ma da yan mata da samari shin kuna sane da cewa HAJIYA FUSAM ta shirya tsaf domin gwangwaje ku da turarakunta masu dankaran kamshi? Tare Kayan gyaram jiki na musamman ,wanda daga nesa kamshin ki kadai ya wadatar ya isar da sakon zuwanki waje,gidan ki kuwa sai ya zam abun kwatance wajen kamshi, kar na cika ku da surutu bara in fara zayyano su_ Farar Humura Bakar Humura Humura special, humura de bain Humura epicé Lait de nuit Parfums désodorisant Parfums rideau et dras Lait de nuit Alkam Kulakcam *Waɗannan kadan ne daga bangaren turaran ruwa* Gagab, sandal flex, Durot, durus, sandal fleur, tafarce, farce, sandal bangui, sandal, hypotonic sandal, al'ut, coktail creation VIP, Gajiji, Mankaji, turaran wutar labule da cafet, Aba malan, boulettes *Munada bangaren gyaran jiki kamar haka:* mai mai saka santsin jiki, mai mai kanshi, Kayan gyaran jiki mai saka fata ta yi santsi da laushi, kayan gyaran jiki mai saka fata ta yi fari, Sabulu mai saka fata ta yi haske, sabulu mai saka fata ta yi santsi, sabulu mai goge yanayin fata, mai wanda baya saka fari mai gyara fata Sayen na gari mai da kudi gida,sai an gwada akan san na kwarai💃💃 Hajiya Fusam na zaune a kasar Niger domin yin magana da ita kai tsaye tuntuɓi wannan number 97 82 44 94 *SECRET DE LA FEMME DU MANGA* Gidan Kamshi, Sirrin Manyan Mata💃💃💃💃💃 Tunda ta fita a hankali ya samu hannayensa da danna computer dake gabansa ta hasko masa step step na asibitin baki daya, a hankali ya danna wanda ya ji yana da bukatar ganni sannan ya dan zuba ido yana kallon, haka kuma kunnayensa na wajen abokanan aikinsa dake aiki karkashinsa sunna zantawa kan abinda ya shafi aikinsu A hankali ya dauke dubansa gannin ta shiga cafetariat din ya kai dubansa wajen da Yumnah ke zaune Irin kallon da take masa ya saka shi dan lumshe mata ido sannan ya mata alamar yaya? Murmushi ta sakar masa tana dan dauke dubanta, domin a zaman nan hauda mata jinni ne yake yi yana sauke mata tamkar hawan cenjin Naira da sauka, aiken nan da ya yiwa Khausar cike da basarwa ya matukar birgeta, sai dai tunanin wani abin kuma ya girmami wannan a zuciyyarta Mintunna ƙalilan Khausar ta dawo hannayanta dauke da baban basket Docter ce ta amsa dan haka ta karasa gaban table dinsa ta mika masa katin cike da kokari da kwarin gwuiwar da ta ba kanta ta ce" Ga katin" A hankali ya dauke dubansa a kanta, da ido ya mata alamun ta ajiye saman table din Da kyar ta iya cije lebenta ta Hanna kanta wani motsin da zai falasata ta ajiye katin sannan ta juya da nufin tafiyarta "Ki je da Madam, ki aunata, bata da lafia " muryarsa ya sake katse mata hanzari Sai da ta rintse idannuwanta, da kyar ta iya hadiyewa ta dakata har Yumnah ta gama shan kanshinta ta fito sai bubudewa take yi suka nufi labo A lokacin da Khausar ke kokarin fitar da abubuwan bukata Yumnah na murmushi ta ce" Ai da kin barshi, ciwon nawa ba wani sai an auna na, furen soyayya na fara tsinka, wanda ya fi komai daraja da kowa a duniyar Mijina, wanda ya bani tun ranar da na zama halaliyarsa, ba kariya dan kar na samu baya kuma jin kunyar hakan!" Har ga Allah, bata taba jin bacin rai irin na wannan lokacin dangane da rashin da'ar yarinyar nan ba Hatta allurar dake hannunta sai da ta subuce ta fadi Ba tare da ta bi ta kan allurar ba ta zubawa Yumnah ido, sai kuma ta zagayo a hankali tana sake Binta da kallo daga sama har kasa Da kula sosai ta ce" Yumna, AKOY wata matsala tsakanina da ke ne wace ban san da zamanta ba?" Yumnah ta wani gyatsine fuska ta ki bata amsa Wani irin makuku da ya tsaye mata a wuya a lokacin sai ta ji koda korarta za'a yi yau saboda Yumnah a shirye take ta amshi korar Rai bace ta damki hannun Yumnah ta juya da ita tana janta ta nufi office din nasa da ita, idannuwanta sun riga sun rufe ta manta waye shi a nan, kuma WACE Yumnah a duniyarsa Tana buɗe office din su docter zasu fito Bata tsaya bi ta kansu ba ta idasa shiga idannuwanta har ruwa ruwa suke da yaji yaji da karfi ta karra janyo Yumnah wace ke tirjewa gabanta na faduwa ta tsayar da ita a gabansa Da mamaki su docter ke neman dawowa, sai dai tunda ya ga abinda yake faruwa dama ya zubawa camerar ido lokaci daya kuma ya masu alamar su tafi da hannunsa sannan ya danna abin rufe office din ya rufe da kansa ya sake zuba mata ido tasa zuciyar shima tana wani iri kamar wanda yake cike da tsoron abinda zai fito daga bakinta dan irin yadda kirjinta ke sama yana kasa sai da ya ji nasa kirjin shima yana hakan A rikice ta dube shi sannan ta kalli Yumnah ta ce" Bama zan tsaya jin abinda ke tsakanina da ke da ya sa kike min abubuwa na rashin da'a ba, da shi din zan yi kuma daga bakinsa nake son ji! , TAUFEEK me matarka ke nufi da magangannu wasu iri da take aika min tamkar Ni din abokiyar gabarta ce ko wani abin ya shiga tsakanina da ita? Haka ranar da na je nemanka yarinyar nan ta min tsaki da wasu abubuwa mararsa dadi, yau kuma kace na aunata tana fada min furen soyayya ta tsinka na halar wanda ba'a saka abinda za'a hanna daukansa? Ni fa yar Hausa ce ba bagwariya ba, kuma abinda take nufi da Ni ina daf da ganewa harma ina jin kamar zan mutu da haushinta in kuwa haka ne!" Fada take hawaye na gama cika idannuwanta ta kalli Yumnah wace ta gama sarewa duniya daga idannuwan mijinta ta ce" Ke kuwa, wace irin shashasha ce da zaki yi tunanin abokina zai iya zamtowa abokin aikata masha'ata? Ko ba haka kike nufi ba kar na maki karya na kulaceki?" A rikice Yumnah ta Dube shi, ta kuma dube ta ta ce" Aunty Khausar Ni kuma?" Khausar ta dantse lebenta sai ga wani hawaye wani na bin wani sunna bin kuncinta, a raunane ainun ta ce" Ni ba mazinaciya bace, Allah ne shaidata, ba komai tsakanina da mijinki sai zumunci gayanan ki tambaye shi, shikennan dan na zama sharar shanye sai a ringa wulakanta ni? Ba za'a barni na ji da ciwon dake ZUCIYATA ba sai an rikita min lisafi? .... TAUFEEK me yasa ne? Me na yi da zafi ne?, Me yasa TAUFEEK kowa idan ya mike yake kokarin ganin ya wulakanta ni bayan na kasance mai kare mutuncina?......" Ta idasa a matukar raunane, a hankali ta dafe kanta jin irin juya matan da yake yi ta juya tana cire rigar jikinta dan kuwa ta sani ne wannan asibiti yau ko ta aba ce ai an koreta kennan dan ta san ta yiwa oga fitsara an gama Kofar take kokowa da ita dan ta budu ama sam kofar ta ki ta budu Ta ja ta ja ya fi a irga ama kofa ta nuna bata san tana yi ba A rikice ya juyo dan neman agajin a bude mata , sai ta ga Yumnah ta nufi dakin da yake na cenza suturarsa ta shige da dan sauri shi kuwa yana tsayen nan yana kallon gefe fuskarsa ta yi wani irin kicin kicin kamar ba TAufik din HAJIA ba A hankali ya kawo dubansa inda take tsaye kikam gabanta na dokawa tana ta nazari kala kala Da hannunsa daya ya mata alamun ta zo nan, hakan ya sa ta dan wara dubanta tana kallonsa da son karrin bayani Lebensa ya sake dantsewa ya mata nunin ta zo inda yake nufi, ama Khausar ta ki aikata hakan A hankali ya cire tishu ya dan goge fuskarsa sannan ya jefa shi cikin abin shara ya mike tsayinsa da kyau ya nufo inda take tsaye Tunda ya taho Khausar ta samu kanta da kallon gabas da yama, kudu da arewa cikin tunanin ina wajen buya ba tare da ta gane haka take tunani a ranta ba A hankali take ja ba, TAUFEEK na matse mata waje har ta kai jikin kofar nan ta rintse idannuwanta da karfi bakinta na bari ta ce" TAUFEEK dukana zaka yi?" Bakin dake bari ya zubawa ido, a hankali ya sake kure mata duba kafin ya bude bakinsa a hankali ya ce" *Kai matsa Bama son haka fa🙄🙄🙄😒* 💔💔💔💔❤‍🩹❤‍🩹💔💔💔💔 *DA CIWO A ZUCIYATA* 💔💔💔💔❤‍🩹❤‍🩹💔💔💔💔 _MALLAKIN_ *SAJIDA NIJAR* *FREE BOOK NE* 3️⃣5️⃣ *GARABASA, GARABASA, PROMOTION, PROMOTION DIN LITATAFAN MARUBUCIYAR A KAN FARASHI MAI SAUKI 1K, YAN NIJAR KUWA 1000 FRANCS CEFA* 1: Duk karyar kada 2: Yar mahaukaciya 3: Neman na kaina 4: Bani da zabi 5: Bak'a ce 6: Kutkale 7: Makauniya ce 8: Mage 9: Duk nisan jifa 10: Idan ka raina inda kake 11: Dutse 12: Alkalamin kadarata 13: Bani da zabi 14: Dakika Biyar 15:Wata kokowar 16: Aure yakin mata 17: Ni zan ladabi 18: Daga tafia daukar soja *Dukansu a kan farashi mai sauki, zaka saka dubu guda ne domin promotion ne nake yi, ka tuntubeni kan layina kamar haka +227 93 81 16 18, Sajida Nijar* Now *Da CIWO A ZUCIYATA* *Tallah, tallah, tallah* *SECRET DE LA FEMME DU MANGA* _Gidan Kamshi, Sirrin Manyan Mata, nesa tazo kusa,Amarya ,Uwar gida,Ango da mai gida Har ma da yan mata da samari shin kuna sane da cewa HAJIYA FUSAM ta shirya tsaf domin gwangwaje ku da turarakunta masu dankaran kamshi? Tare Kayan gyaram jiki na musamman ,wanda daga nesa kamshin ki kadai ya wadatar ya isar da sakon zuwanki waje,gidan ki kuwa sai ya zam abun kwatance wajen kamshi, kar na cika ku da surutu bara in fara zayyano su_ Farar Humura Bakar Humura Humura special, humura de bain Humura epicé Lait de nuit Parfums désodorisant Parfums rideau et dras Lait de nuit Alkam Kulakcam *Waɗannan kadan ne daga bangaren turaran ruwa* Gagab, sandal flex, Durot, durus, sandal fleur, tafarce, farce, sandal bangui, sandal, hypotonic sandal, al'ut, coktail creation VIP, Gajiji, Mankaji, turaran wutar labule da cafet, Aba malan, boulettes *Munada bangaren gyaran jiki kamar haka:* mai mai saka santsin jiki, mai mai kanshi, Kayan gyaran jiki mai saka fata ta yi santsi da laushi, kayan gyaran jiki mai saka fata ta yi fari, Sabulu mai saka fata ta yi haske, sabulu mai saka fata ta yi santsi, sabulu mai goge yanayin fata, mai wanda baya saka fari mai gyara fata Sayen na gari mai da kudi gida,sai an gwada akan san na kwarai💃💃 Hajiya Fusam na zaune a kasar Niger domin yin magana da ita kai tsaye tuntuɓi wannan number 97 82 44 94 *SECRET DE LA FEMME DU MANGA* Gidan Kamshi, Sirrin Manyan Mata💃💃💃💃💃 Bakinta dake bari ya zubawa ido sosai, a hankali ya sake kurewa fuskarta duba kafin ya bude bakin kasa kasa sosai ya ce" Menene wanann?" Khausar ta yi gagawar lumshe idannuwanta sakamakon iskar bakinsa da ta dan shafi saman fuskarta a hankali har ta ji kanshin abin amfanin gyaran bakinsa, maganar kanshin jikinsa kuwa ji take kamar itane ta yi wanka da turaren, irin matsewar wajen nan ita da shi tunda suka hadu basu taba samun irinta ba Khausar ta yi ta yi ta gane mene din a cikin tarin fitsarar da take nadamar dama bata masa ba wane yake tambayar menene din ta kasa ganowa dan abinda ta fada da yawa ai kau? A sanyyaye ta dan dago idannuwanta tana marairaice murya dan alkur'an du sai take tunanin wai kar fa ya zaneta fa, a raunane ta ce" Dan Allah ka yi hakuri, dama Mama ce tace yau na tabatar na baka hakuri , to dama WANCEN yar ce ta raina Ni take min wasu abubuwan fa shine na ga ai ta rainani kau, kuma magangannunta dai ba dadi sosai dan kamar wace ke zarginmu bayan Ni da kyau haramun din junna ne, ka yi hakuri ba zan kara ba besty" Irin yadda ya yi maganar muryarsa a kurya ainun, haka ta bashi amsa, irin maganar nan ta cen cikin nan kana yi tsigar jikin mutum na tashi wace har ga Allah makocin daki aka cika yiwa itama a maganar salihan bayi Maganarta take yi harda yar kwalarta , fatan da take ya matsa koda da taku daya ne ai inma a dakun ne zata fi shiryawa ba a shamaceta a nadeta ba ko? Ko ba komai mutumen nan kato ne, kato irin kartin nan masu tsayi da cika, yana iya fin karfin mata ai A hankali ya kai yatsarsa daf da lebenta, sam ba da niyar tabawa ba, sai dai yana kaiwa din yatsar tasa ta dan dangwali abinda ke bakinta yake walwalwal kasa kasa ya ce" Ni ba fitsarar ba, yau kika fara min rashin kunya ne? Wannan abun da kika saka a bakinki menene kuma?" Kashhh alkur'an sai da ta ji salama a birnin zuciyyarta, harda sau dan yin dage dan tana so ko kafadarsa ne tsayinta ya kai ko a yi magana ta sako da sako mana, ama a haka kamar abin ya fara haramta matsewar wajen, duda ba jikinsa ke gogar nata ba, ama kuma hucin junna da suke shaka ai ba halal bane! Dan murmushi ke son kubce mata ta wani dage gira ta ce" Jan baki Kennan , haka sunnansa" gaba daya tana kokarin manta fushin ta da bacin ranta da ta kunsa a kansa, har ji take kamar zata saki murmushi dan sunna zantawa haka Baki ya tabe ya laluba aljihunsa yana janyo dan karamin tissu fari Kal kal ya dan nufi bakin nata da shi a hankali ya ce" Khausar kwaliya bata maki kyau , ki daina, kuma kin ga shigar nan itama sam bata yi ba kin ji?" Har zafi zafi leben nata ya fara mata ta saka hannunta tana rike nasa a hankali ta janye tana ta kokarin dan jan yaji kadan dan zafin da leben ya fara, a hankali ta ce" ka daina zafi zan tsotse abina, TAUFEEK kaine fa baka son kwaliya , Ni YANZUN ai kaunarta nake, kuma ka ga Salisma yace ashe haka nake da kyau, bai taba ganin doguwar riga ta amshi mutum ba sai a kaina........" Sai da ta karashe wai kuma kunya ta kamata, da sauri ta rufe idannuwanta ta bi ta kasan hannunsa da ya dan dafe kofar da shi ta tafi wajen kujerar nan mai tsayi lafiyayiya ta zauna tana murmushi cike da jin kunya dan wollah maganar nan ta bata kunya, batama san cewa ta yarda wani ya ji ba sai gashi tana fadawa TAUFEEK A kala ya dauki minti daya a tsayen nan yana mamakinta, what? Har irin maganar nan take yi da wani bakon rayuwarta? Ya Salam! Wajen ya karaso ya zauna ya bi irin zaman da ta yi da kallo ya ce" KHausar, har wannan maganar kike yi da katon banza?" Da mamaki KHausar ta dago tana kallonsa ta ce" Taufeek salis din ne katon banza?" A kure ya ce" To ƙatuwar banza ce?" Khausar ta girgiza kai da sauri, sai kuma ta dan matso kusansa sosai kamar yadda takan yi idan zata masa magana mai mahimmanci ta ce" TAUFEEK, yana so na fa sosai, maganar da nake maka a yau dai Inaga zasu gana da mahaifinsa da Aba, yace aure yake so kafin ya yi tafia yake so a daura shi, kuma nima ina sonsa sosai ai" 'Dan Allah ki ringa tauna maganar bakinki haka!, Ke yanzu daga zuwan mutun rayuwarki har kike magana irin wannan da shi? Me Kennan? Au aure yake so? Yana dai son wani abin kuma bai isa ba, maganar kina sonsa kuwa wannan ai karyar banza da wofi kike yi, shirme sai an yi magana ki isheni da faman *DA CIWO A ZUCIYARKI* ke har kin san mene ciwon meye kuma zuciyar? ' "TAUFEEK?" Khausar ta katse masa masifafen fadan da ya dauka a cikin zuciyarsa har ya dawo da dubansa saman fuskarta yanai mata kallon jin haushi Kai ya girgiza a hankali ya jinginar da bayansa jikin kujerar ba tare da yace da ita ci kanki ba Shiru ta yi na yan dakiku, sai kuma ta tabe baki tana dauke kanta daga sajen fuskarsa sannan ta turo baki tana mai jin haushin kanta, ba dan komai ba sai dan gannin dan sirrin da ta rika itama ta ce sai dai ya ji a duniya ta zauna ta kwashe ta sanar masa rabi ba tarema da ya tambayeta ba, sam wannan hali nata baya mata dadi haushin balaki yake bata wollah Mikewa ta yi ta saka takalmanta bakin nan a tunzure ta dauki rigarta ta yafa a kafada sannan ta juya zata wucewarta "Ina zaki je?" Ya iya budar bakinsa da kyar ya tambayeta ama bai bude idnanuwansa ba Lekawa take dan ta gane ta inda ya san zata tafin, sai kuma ta koma ta tsaya tana sake turo baki ta ce" Gida zan tafi ne" Sai yanzu ya dago dubansa a nutse ya kalli agogon office din sannan ya kalleta yana ragewa idanunsa girma ya ce" kin tashi ne?" Itama agogon ta duba, ta ga da sauran kusan awani biyar koda zata tashin Girarakinta ta tatare tana dan son tunzuro bakinta ta wani langwabe kanta gefe tana kallonsa da alamun rarashi A hankali ya dan girgiza kansa yana sakin dan murmushi ya ce" Me zaki yi a gidan idan kin je?" Khausar aka wani kifta ido ta ce" Dama dan sahuna yau ya je kauye ne, sai Salis yace idan na gama da wuri zai zo ya kaini gida in ya fito daga wajen aiki" TAUFEEK ya dan gyada kai ya sake girgiza kan nasa ya ce" To albashina za'a ringa ci ana wasa da aiki Madame?" Khausar ta Dube shi, sai kuma ta saki murmushi tana tuna abubuwa da yawa a ranta, Allah mai alheri wai ashe gagarumin likita ne, Uhum lalle Rigar ta bude ta shiga sakawa tana dan murmushin da ya ki barin fuskarta har ta saka ta dan dube shi ta ce" Na koma Sir" Shima murmushin ya yi yana kallonta har ta juya a hankali ya ce" Kuma Ni ne zan kai ki gidan" Daga haka ya yi shiru ya dauke dubansa a kanta har ta gama yar tsayuwarta ta wuce Mikewa ya yi a Nutse ya karasa dakin nan ya bude ya shiga Tarar da ita ya yi ta yi wani irin zama kanta a saman kaffafuwanta , kuka take yi ne ko me tana dai ta girgiza jikinta yannayinta sam babu dadin gani A Nutse ya karasa inda take ya zauna gefenta ya saka hannunsa ya janyota jikinsa a hankali ya zuba mata ido yana gannin yadda ta rukunkume shi ta saki kuka a birkice ta shiga bashi hakuri da kuma fadin" Dan Allah kar ka ce min kana son ta, Bara na fada maka maganar gaskiya ina matukar kishinta, ina kishinta, kishin Kausar nake yi fiye da kowace mace da zata iya rabarka, dan kuwa a yadda kake nunawa Khausar kula da dukkan abinda nake gani idan har maganar soyyaya ce tsakaninka da ita Ni na san ta rabani da mijina Kennan har Abada, Taufeek ka fada min soyaya kuke yi ne?" Ita ke maganar shi ke jin hankalinsa na karra tashi a kan maganar, soyayya? Wace irin siyaya, Gannin halin da take ciki, gashi kuma shi dama tun jiyan nan ya gama gane tana dauke da junna biyu ne ya sa a Nutse ya riketa sosai a jikinsa dan ta daina mugun motsin da take yi kar ta jima kanta rauni, du irin rukunin bacin ran da ta hadasa masa ya yi iya yinsa ya danne, dan kuwa bacin ran da yake ciki ba zai sa ya danne yannayinta ba, abu daya ya sani a furucinta baban abinda zai iya dakatar da tafiyarsa da ita take dauke da shi, watau tana zarginsu ne da Khausar, in kuwa hakane lalle Yumnah bata da wayo kuma wajen soyayar da take masa ba yau ba ya tsaya iya kunnensa, dan idan har so din kake, dole zaka jure wasu abubuwa na mutun, Bama zaka iya ganninsu a matsayin laifi ba, ba kuma zaka ringa harinsa cikin jahilci ba Sai da ya ga ta dan nutsu ama kuma tana matukar son jin amsarsa ya mata biris ya mikar da ita tsaye a Nutse ya ce" Ki wanke fuskarki a kai ki gida" daga haka ya juya ya fice a dakin Yumnah ta dauki lokaci mai tsayi a bayin nan cikin halin tunani kala kala Babu abinda ke rudar mutun irin jiran fada ya ji shiru Bata san me hakan ke nufi ba, ta kuma san ta aikata baban laifin da baya so wanda wannan banzar ta zo ta fada kai tsaye , watau zarginsu take Da kyar ta iya fitowa ta maida hijab din ta ta fito Nan ta samu direba da wata nurse rike da abincinta suka mata jagora suka wuce Sai da suka tafi ya dawo office din ya nemi waje ya zauna a hankali ya dafe gaban goshinsa dake masa barazanar tarwatsewa Tarin abinda ke cikin ransa ya masa yawa Yana tare da gagarumin *CIWO A ZUCIYARSA* wanda ya rasa ta inda zai kamo Ba dan komai ba sai dan zuciyarsa da ta ki bashi amanar hakan A hankali ya mike ya koma saman kujerar nan ya kwonta yana kankame jikinsa dake masa wani iri, shi kadai ya san a irin gabar da yake kai a wannan lokacin, baya tunanin idan ya riki mace ko wace zata samu kanta cikin sauki a hannunsa, shi yasa ya nisanta kansa da wace take halalin nasa dan gudun kar ya raunatata ________________________________ Tunda Elhaji ya gama maganar nan Aba ya dafe haba cike da matsanancin mamaki ya kasa furta koda A ne yana kallon Elhaji Yar dariya Elhajin ya yi yana jinjina kansa ɗan tabbatar masa da maganar da ya fada din, ama kuma Aba ya kasa furta koda a ne Elhaji ya ce" Elhaji Mamuda ko dai na zo a lati ne?" Aba ya ja numfashi yana jinjina kansa cike da mamaki ya ce" .... Ga breakfast 😁😁😁😁😁 💔💔💔💔❤‍🩹❤‍🩹💔💔💔💔 *DA CIWO A ZUCIYATA* 💔💔💔💔❤‍🩹❤‍🩹💔💔💔💔 _MALLAKIN_ *SAJIDA NIJAR* *FREE BOOK NE* 3️⃣6️⃣ *GARABASA, GARABASA, PROMOTION, PROMOTION DIN LITATAFAN MARUBUCIYAR A KAN FARASHI MAI SAUKI 1K, YAN NIJAR KUWA 1000 FRANCS CEFA* 1: Duk karyar kada 2: Yar mahaukaciya 3: Neman na kaina 4: Bani da zabi 5: Bak'a ce 6: Kutkale 7: Makauniya ce 8: Mage 9: Duk nisan jifa 10: Idan ka raina inda kake 11: Dutse 12: Alkalamin kadarata 13: Bani da zabi 14: Dakika Biyar 15:Wata kokowar 16: Aure yakin mata 17: Ni zan ladabi 18: Daga tafia daukar soja 19 : ZAKIN SARAKAI *Dukansu a kan farashi mai sauki, zaka saka dubu guda ne domin promotion ne nake yi, ka tuntubeni kan layina kamar haka +227 93 81 16 18, Sajida Nijar* Now *Da CIWO A ZUCIYATA* *Tallah, tallah, tallah* *SECRET DE LA FEMME DU MANGA* _Gidan Kamshi, Sirrin Manyan Mata, nesa tazo kusa,Amarya ,Uwar gida,Ango da mai gida Har ma da yan mata da samari shin kuna sane da cewa HAJIYA FUSAM ta shirya tsaf domin gwangwaje ku da turarakunta masu dankaran kamshi? Tare Kayan gyaram jiki na musamman ,wanda daga nesa kamshin ki kadai ya wadatar ya isar da sakon zuwanki waje,gidan ki kuwa sai ya zam abun kwatance wajen kamshi, kar na cika ku da surutu bara in fara zayyano su_ Farar Humura Bakar Humura Humura special, humura de bain Humura epicé Lait de nuit Parfums désodorisant Parfums rideau et dras Lait de nuit Alkam Kulakcam *Waɗannan kadan ne daga bangaren turaran ruwa* Gagab, sandal flex, Durot, durus, sandal fleur, tafarce, farce, sandal bangui, sandal, hypotonic sandal, al'ut, coktail creation VIP, Gajiji, Mankaji, turaran wutar labule da cafet, Aba malan, boulettes *Munada bangaren gyaran jiki kamar haka:* mai mai saka santsin jiki, mai mai kanshi, Kayan gyaran jiki mai saka fata ta yi santsi da laushi, kayan gyaran jiki mai saka fata ta yi fari, Sabulu mai saka fata ta yi haske, sabulu mai saka fata ta yi santsi, sabulu mai goge yanayin fata, mai wanda baya saka fari mai gyara fata Sayen na gari mai da kudi gida,sai an gwada akan san na kwarai💃💃 Hajiya Fusam na zaune a kasar Niger domin yin magana da ita kai tsaye tuntuɓi wannan number 97 82 44 94 *SECRET DE LA FEMME DU MANGA* Gidan Kamshi, Sirrin Manyan Mata💃💃💃💃💃 Aba ya ja numfashi yana jinjina kansa cike da madaukakin mamaki ya ce" A'a Elhaji, ko daya, idanma AKOY din gaskiya Ni dai ban san maganar manya a ciki ba, bayan wannan Khausar ai budurwa take ba bazawara ba, alhakin zaba mata miji a kanmu yake mu iyayenta miji na fari, abinda nake roko daya ne tal a bani dama na je na fadawa Allah sannan na sanarwa mahaifiyarta, ko menene na san zai zo da wurin ama a bani kwana uku na je na kadaice kaina na barawa Allah zabi, na san ai zaka dauki sati biyu zuwa uku kafin ka tafi ko?" Elhaji ya bashi amsar cewa eh zai dauka, daga karshe suka ajiye maganar nan da kwana ukun Aba zai sanar masa abinda ya tsayar, tsayawar kuwa a kan abu daya ne daidaito kan daurin auren KHAUSAR din, maganar biki zata biyo baya ne da yardar ubangiji da maganar tarewa Tunda Aba ya shigo gidan fara'ar fuskarsa ta kasa boyuwa , har sai da Mama ta gaza hakuri ta yi tambayar shin me aka samo ne mai girma haka? Duda kasancewarsa mutun mai sakin fuska da fara'a, ama ta yau din baba ce sosai Bai boye mata komai ba ya sanar mata, sannan ya bata damarta itama ta uwa kan ta sanarwa ubangiji ya yi masu zabi na aalkhairi Sosai itama ta cika da yannayi na farin ciki da kuma fata mai kyau, ta sani ne idan Allah ya yi an yi abin a yanzu dama shine mijin Khausar din sai yanzu ya bayyana, dan haka itama ta kame bakinta ta shiga sanarwa ubangiji, sai dai abu daya tak da ta gabatar kamar yadda Aba ya sanar mata shine dogon zaman da suka yi bayan sallar asubahi ita da Khausar, zaman ya kunshi magangannu irin wanda Khausar din ta jima da yi, cewa ta jima da bada wuka da nama a hannun mahaifinta kan ya zaba mata mijin aure, tun daga lokacin da ta fara sarewa lamarinta da soyayya ta yi wannan sadakarwa, Sosai abin ya zo mata wani iri, domin ba'a kuma maganar nan ba tunda ta sanarwa iyayenta cewa ita ko wanene in dai ya kwonta masu a zuciya to ita din mai biyayya ce, daga nan basu kuma tada magana makamanciyar wannan ba, nan da nan ta sakawa ranta cewa eh lalle da gaske Salis yake bai zo da wasa ba kamar yadda ya sanar mata, ya fada mata cewa zai turo mahaifinsa da wuri a tsaida komai dan yana so a yi komai kafin tafiyarsa, a cen kasan zuciyarta babu abinda ya cika mata zuciya sai tarin farin ciki da zumudi da kuma adu'ar Allah ya nuna mata ya kuma tabbatar mata da alkhairin hakan, ta kuma tabatarwa iyayenta cewa tana kan bakanta, koda a rashin sani aka daura mata aure ya dauru dan su suke da ita ba ita take da su ba Daga nan ta shirya ta wucewarta wajen aiki, zuciyyarta cike da tunani kala kala , abinda ya fi komai tsaye mata a rai shine farin ciki, sai dai ko TAUFEEK ba zata sanarwa ba , sai ta ga abinda yake faruwa ya tabbata kafin kowama ya ji, Haka ta wuni aiki cike da tunani har yama ta yi ta juya gida a ranar ko haduwama basu yi ba da Taufeek dan bai shigo asibitin ba, sai dai tana ji a cen kasan zuciyarta da wahala yauma ta iya kwontawa ba tare da ta dan sanar masa abinda ke tafe ba, ta rasa ta yaya take iya wannan abin, sam bata san wani abu wai shi sirri tsakaninta da shi ba, ga yan uwanta mata dai, sai ta boye masu abu dubu bata boyewa TAUFEEK ba _____________________________________ Firar dare suke yi su uku a saman baban filin wajen hutun Aba, watau da Aban, da HAJIA sai TAUFEEK Kusan firar ta fi yawa tsakanin TAUFEEK da Aba, domin Hajiar zaune ne take sai kada kafa take yi abinda ke bakinta mai yawa ne ama zuwan TAUFEEK ya sa ta kame baki dan yana mata fadan irin hakan, yana hannata kawowa mahaifinsa karar matansa, bayan ita tafe take da magana mai mahimmanci ta abinda bata tunanin zai haifi ɗ'a da ido, domin ita ke gannin take taken iyalinsa a kan sarakuwa daya tak da ta fara shigowa gidan, yarinyar sam bata da wayo, in ba rashin wayo ba ta yaya zaki zo gidan da sarakuwarki a ciki ama tsakaninta da ke in ta sauko ta ganki ku gaisa shikennan, koda yaushe kina nanike jikin kishiyoyinta kina aikata me Kennan? Da ace kin tarar da wata fahimta bayananiya da sai kice ai kansu hade kika tardo su, ba'a hannaki musu biyayya ba ko yin zumunci da su da zama inda suke ba, ama ta yaya zaki fifitasu a kan mahaifiyar mijinki? Dama ita HAJIA kaka ba ta kanta take ba dan kuwa Yumnah ta gaisheta bata gaisheta ba du ita ta gano, ama mahaifiyar taufeek da ta zamto kunnu huce in shaka ba zata yarda a ringa raina mata wayo ba gaskiya, shi yasa take zaune sai sake hade baki take tana turowa cike da gundura da jin firar tasu, kuma ta tabbata da gaya Magidanci ya ki basu waje suke firar kasuwanci shi da ubansa, dan ya san mai kwanoni da son fira da shi yake takalo maganar nema, ai kam yau ko ita ko su an ga wanda zai gaji dan kuwa a harshen zanninta akoy goro daure tun dazun da ta ji alamun za'a raina mata wayo takan ciro ta kantsa sannan ta daure tana binsu da kallo da harara Wayar Aba karama dake kuka ce HAJIA ta kawo masa, da kyar take tafia domin a dazun anma zata zata haihu ne sai kuma nakudar ta dan lafa, ama yanzu haka cikinta take shi yasa ta tahowarta bangaren mijinta dan ba wani yarda zata yi dayarsu ta ga gazawarta a wajen nakuda ko haihuwa ba bale kishiya ta yadda mata magana Wayar ya amsa yana mikewa ya dan yi gaba, dan maganar da zai yin yana bukatar ya dan matsa Jim kadan ya dawo yana dan murmushi gannin Hajia ta sakar masa harara tana dauke kai ta dubi TAUFEEK ta ce" Wai Ni ko meye abin munafurci a waya kuma? Salon a yi gaba a yi da ni, to ahir dinka inma aure zaka yi ba dai uwar Magidanci zaka karawa ba , ah to , ko mema yace a wayar Allah na tuba?" Taufeek ya hade fuska yana mata duban nan nasa idan tana abinta tana sako ubansa, hakan ya sa ta sake tabe baki ta dauke kai ta ce" Dadin abin mai kwanonn nice nan babarsa ba wancen sanyi karai din ba, ina da damar daukeshi da mari in ta raya min babu mai ce min na marar masa d'a ehe!" Aba ya saki kawatacen murmushi yana kaiwa zaune ya ce" Allah ya huci zuciyarki HAJIA, dama maganar auren KHAUSAR ne " A tare da ita da TAUFEEK din suka zuba masa ido, sai dai cikin ikon Allah Aban ya kame bakinsa ya shiga dan duba wayar hannunsa Kallonta TAUFEEK ya yi a hankali gannin ta yi shiru bayan Aba dai ai d'anta ne kuma ya fara magana ya yi shiru bai gama ba? Ai Bama kyau fara zance a kyale, HAJIA kuwa da kufula ta karɓe wayar Aba sannan ta nuna shi da wayar ta ce" Kai zaka bani magana a bude a bayyane ko sai na rotsa wayar nan ne Ni?" Aba ya zuba mata ido, sai kuma ya saki murmushi ya ce" Au, HAJIA dangane da maganar auren KHAUSAR din ?" HAJIA ta gyada kai ta ce" Eh mana da nawa?" Aba ya girgiza kansa da sauri ya ce" dama maganar ce mahaifinta ya sanar min cewa nan da yan kwanaki goma haka za'a daura mata aure ta samu miji a anguwarsu" Kusan a tare bakin HAJIA da TAUFEEK suka yi magana, TAUFEEK da subutar harshe ya ce" Khausar din?" HAJIA kuwa lokaci daya ta shiga sallalami tana tafa hannu kafin ta debowa TAUFEEK wani duba tun daga ƙafarsa har kansa ta watsar ta rafka tagumi ta ce" ka cucemu, ka gama cutarmu, sai ka shirya tun gobe mu je kasuwa Ni da kai mu ciro anko mu maidawa kura aniyarta , daga nan ka kaini wajen masu kayan ganye in hado hade hade na tsumi mu zo in tafasa mu kai mata ta shiga sha dan tsumi iya tsumi sai na tsumata alkawari ne na yi kuma cikawa ya zame min tilassss!, Kai wannan yaro wannan yaro da kake gani ka haifi durum baki a dinke , kai yanzu wannan hali ne? Da WANCEN abar a bushe uwa karauki zaka gama rayuwa? Ama ba'a more aure ba sam, kuma ba'a gaji uba ba, kai ko koyi na zaka yi da mahaifinka ba? Siririya daya ya yi ya ga ba riba ya ajiye, yanzu idonka idon Khausara wani zai dauka? Dubata fa cinyoyin nan ko na sa albarka, bayanan kuwa tas kake ajiye faranti ya zauna......." Idannuwansa ya lumshe a hankali sakamakon yadda amon Muryar HAJIA ke amsa masa a kwakwaluwarsa Da kula ya sake zuba mata ido a karro na biyu yanai mata alamun ta iya bakinta ama zuba take tana fada har tana neman share hawaye, d'anta kuwa na bata hakuri cikin ikon Allah A hankali ya iya saka takalmansa da ya cire ya dora ƙafarsa saman abinda ta shinfida ta zauna ya mike cikin kula da yannayinsa ya juya dan sai ya ji sam surutun ne baya so "TAUFEEK?" Aba ya fada yana dubansa da dan mamakin yannayinsa, duba da yanzu yanzu suke firarsu a sake yadda suka saba Juyowa ya yi dan amsawa sai ya ga shi din suke kallo, hakan ya sa ya sakar masu murmushi yana dan sosa goshinsa a hankali ya ce" Aba, inada wani aiki ne ashe yanzu na tuna, good night" Aban ya amsa shi da Allah ya tashe su lafia sannan ya tafiyarsa ya bar Aban da HAJIA na tatauna wata muhimmiyar maganar A daren nan, wani irin ciwon kai mai masifar zafi ne ya sauko masa, wanda ya danganta shi da rashin isashen barci ne kwana biyun da baya samu, dan haka ya yi iya yinsa dan ya samu hutun ama sam barcin ya ki zuwar masa Lokaci kankani ya samu kansa cikin yannayi na mugu mugun bacin rai kan abubuwa da dama, domin yana dawowa daga sallar asubahi fadan da ya rike bai juyewa Yumnah ba ya sameta har dakinta tana shafa manta ya sauke mata kwondon balakin da ya tayar mata da hankali, domin tsohuwar maganar da take jin salama a ranta cewar ya manta ce ya taso mata ya sakata gaba ya mata wankin baban bargo da jan dogon kashedi a kan ko da wasa ta kuma gigin wannan banzan tunanin a kansa zata sha mamakinsa, kuma ta kiyayeshi ba auren zobe ya yi da ita ba bale tace zata ringa yanka masa kashedi a kan irin mu'amalarsa da koma waye, bai kuma aureta da alkawarin zama da ita kadai ba dan ko yanzu aure ya kama shi yana iya yi babu yarjejeniyar zama da ita kadai a duniyarsa! Daga nan ya fice ya shige dakinsa ya shiga wanka yana jin wani balaki na Kunno shi Yana fitowa a wankan ya saka fara kal din jalabiyyarsa da dogon wandonta yana fesa turare dan ba zai fita da wuri ba aka shiga buga baban falon Bai tsaya wani bata lokaci ba ya shiga saukowa dan budewa Yana budewa ya saukewa HAJIA idannuwansa da suke rine cike da gajiya da abin barci Kicin kicin ya yi da fuskarsa ya dubeta tsaf ya ce" Meye ? Zuwa kika yi ki kaini ciro anko da menema? Sai ki daukeni, nace ki daukeni , kin ga ki fita hanyata ki bani lafiya in kina so ba anko ba ki ciro Chaina ki laka ama ni ki bani lafiya!" HAJIA ta hangame baki tana kallonsa hadi da gyara tsayuwarta ta ce" Ka ga wani ikon Allah ranar juma'a du Musulmin kirki ai ya farka da fara'a ama banda kai?" Taufeek har zai juya ya juyo ya sake tsareta da harara yana tunanin inama ace wannan din nan dai in ya mata wani abu mai kwanoni ba zai tsine masa ba ? Kwafa ya yi zai juya HAJIA ta sake gyara tsayuwa ta ce" Sai ka daukeni da mari in gane tabata ta sameka, Magidanci Ni din nan da kake gani kadangaren bakin tulu nake, a karni a kar tulu a barni in bata ruwan tulu!, Maganar anko kuma ai ka san dole ne mu fitar Ni da kai dan a ramawa kura aniyarta, YANZUN dai ubanka yace ka zo ga cen wancen tana nakuda mu je mu ajiye masu ita mu wuce kasuwa, kai in ba sai na nuna maka Ni na haifi mai kwanoni ba kace min ba Ni bace HAJIA!" Daga haka ta juya har kamar iska zata dauketa ta nufi bangaren matan gidan sai bambami take tana ambaton ita Magidanci zai gwadawa danyen kai A hankali ya lumshe idannuwansa yana jin harda juwa ke son maka shi a kasss, a Nutse ya koma saman ya gama abinda zai yi ya sanar masu a kaisu asibitin sannan ya kimtsa ya sauko ya shige mota ya bi bayansu yana jin kawai zazabi ne ke damunsa shi yasa yake jinsa wani iri, sai tarin bacin ran da yake kyautata zaton tarawa ne ya yi yake neman yi masa yawa a ransa, Yana fitowa daga motar ya nufi bangaren amsar haihuwar Bai shiga ba domin likitoci ne rufe kanta dan haka ya karasa wajen mahaifiyarsa dake zaune wace rabonsa da ita tun jiya da yama ya gaisheta da kula sosai sannan ya nemi kam su mike su karasa office dinsa idan ta sauka sai su sauko Tun kafin ta bashi amsa HAJIA dake zaune ranta a matukar nace tana sake bin asibitin da kallo zuciyyarta tamkar zata kama da wuta ta dubi bangaren da HAJIA kaka ke zaune tana jan carbi ta sake hade rai ta ce" Ni kam ina nan ai ba za'a barta ita kadai ba" Mama ta yi murmushi ta ce" Ka je kawai ka kama aikinka ai ka ga ba zamu je cen mu zauna ba mu da muka kawo mai haihuwa, nama yi kiran KHAUSAR tace min yanzu zata karaso asibitin ko?" A hankali ya dan dago idannuwansa dake dauke da launin ja, zai bata amsa KHausar ta karaso da salama a bakinta ta karasa wajen HAJIA ta fara gaisheta sai wani washe mata baki take sannan ta karasa wajen su Maman ta duka har kasa tana gaishe su lokaci daya tana ajiyewa Maman dangin su ruwa ne ta dan kalli TAUFEEK dake gefen Mama ta ce" Morning besty, Mama kin ga ruwa kawai na tsaya cen na amso dan ban san da me zaku karya ba, bari in amshi katinsa in koma me da me zan kawo ne na kari na tabbata safiyar nan ba'a karya ba aka fito" HAJIA kaka aka wani saki murmushi aka cira kai kasa kasa ta ce" Aikin banza, ga mace mai mutunci kana rainan hankali yarinya ta san darajar mahaifiyarka kana shirme, mu zuba mu gani dan mai Kwanoni!" 😭 Ina tsoron HAJIA, HAJIA akoy rigima da neman mutun da balaki, sai wasu abu na neman fitina take yi🥹🥹🥹🥹 bayan mu oho sai mema wai☹️🙄 💔💔💔💔❤‍🩹❤‍🩹💔💔💔💔 *DA CIWO A ZUCIYATA* 💔💔💔💔❤‍🩹❤‍🩹💔💔💔💔 _MALLAKIN_ *SAJIDA NIJAR* *FREE BOOK NE* 3️⃣7️⃣ *GARABASA, GARABASA, PROMOTION, PROMOTION DIN LITATAFAN MARUBUCIYAR A KAN FARASHI MAI SAUKI 1K, YAN NIJAR KUWA 1000 FRANCS CEFA* 1: Duk karyar kada 2: Yar mahaukaciya 3: Neman na kaina 4: Bani da zabi 5: Bak'a ce 6: Kutkale 7: Makauniya ce 8: Mage 9: Duk nisan jifa 10: Idan ka raina inda kake 11: Dutse 12: Alkalamin kadarata 13: Bani da zabi 14: Dakika Biyar 15:Wata kokowar 16: Aure yakin mata 17: Ni zan ladabi 18: Daga tafia daukar soja *Dukansu a kan farashi mai sauki, zaka saka dubu guda ne domin promotion ne nake yi, ka tuntubeni kan layina kamar haka +227 93 81 16 18, Sajida Nijar* Now *Da CIWO A ZUCIYATA* *Tallah, tallah, tallah* *SECRET DE LA FEMME DU MANGA* _Gidan Kamshi, Sirrin Manyan Mata, nesa tazo kusa,Amarya ,Uwar gida,Ango da mai gida Har ma da yan mata da samari shin kuna sane da cewa HAJIYA FUSAM ta shirya tsaf domin gwangwaje ku da turarakunta masu dankaran kamshi? Tare Kayan gyaram jiki na musamman ,wanda daga nesa kamshin ki kadai ya wadatar ya isar da sakon zuwanki waje,gidan ki kuwa sai ya zam abun kwatance wajen kamshi, kar na cika ku da surutu bara in fara zayyano su_ Farar Humura Bakar Humura Humura special, humura de bain Humura epicé Lait de nuit Parfums désodorisant Parfums rideau et dras Lait de nuit Alkam Kulakcam *Waɗannan kadan ne daga bangaren turaran ruwa* Gagab, sandal flex, Durot, durus, sandal fleur, tafarce, farce, sandal bangui, sandal, hypotonic sandal, al'ut, coktail creation VIP, Gajiji, Mankaji, turaran wutar labule da cafet, Aba malan, boulettes *Munada bangaren gyaran jiki kamar haka:* mai mai saka santsin jiki, mai mai kanshi, Kayan gyaran jiki mai saka fata ta yi santsi da laushi, kayan gyaran jiki mai saka fata ta yi fari, Sabulu mai saka fata ta yi haske, sabulu mai saka fata ta yi santsi, sabulu mai goge yanayin fata, mai wanda baya saka fari mai gyara fata Sayen na gari mai da kudi gida,sai an gwada akan san na kwarai💃💃 Hajiya Fusam na zaune a kasar Niger domin yin magana da ita kai tsaye tuntuɓi wannan number 97 82 44 94 *SECRET DE LA FEMME DU MANGA* Gidan Kamshi, Sirrin Manyan Mata💃💃💃💃💃 Ita kam Khausar bata san komai ba, Mama kuwa murmushi ke kawace a fuskarta, cike da kular da ta saba ba KHausar in tana kusa da ita take dubanta bayan ta buda ledojin ta ce" A'a, ke da kika zo aiki kuma Khausar ma tsareki a nan? " KHausar ta ce" A'a mama, yau din ai bani da wani aiki dama saloon zan je da wuri na koma gida na samu kiranki, gashi Maman ta fita itama da ta sama min wani abin na zo da shi sai kawai na sayo faro, bari dai in amso abincin" Daga haka ta karasa kusa da shi sosai ta ce" Bani katin" Tunda ya dinke bakinsa kasa kasa Hajia ce yake makawa harara tana maka masa, sai yanzu da ta wani tsaya masa a gaba Aljihunsa ya laluba ya ciro katin ya mika mata da dan mamaki ya bi hannunta da kallo wanda ke dauke da kunshin da bai san da shi shekaran jiya ba Kai kawai ya girgiza a ransa yana ayana' amare Kennan, dole a ringa kwaliya, dole ki tsirarwa kanki abubuwan da ba zasu fisheki ba, wai nine kike boyewa aurenki dan kawai na boye maki aikina???' Zancen zuci yake yi, tsakaninsa da Allah sam bai san a me ya dora idannuwansa ba har wajen sai ido hudun da HAJIA ta juyo suka yi bayan ta raka bayan Khausar da ido ta wani dage gira saya sannan ta saki wani murmushi ta ci gaba da jan carbin da sam bai yarda da addu'a take yi ba wannan tsohuwar mai kwanonin Kai ya dauke yana girgiza kai sannan ya mike ya bi umarnin Maman da tace ya tafiyarsa office dinsa hakan zai fi alkhairi dan baya so yana zaune gefen uwar mutane tana nemansa da fitina gaskiya ga ma'aikatansa ma ko sun durfafo da karfi karfi in suka ganshi sai ka ga sun shiga kame kame kamar wani dodo, KOWAMA haushi yake bashi yau din dan haka ya yi tafiyarsa A kadan sai kusan goma matar Mai kwanoni ta sauka, ta samu baby girl dinta Sai a lokacin Khausar ta nufi office dinsa dauke da ledar abincinsa da bata samu ta mika masa ba tunda ta zo da na su Mama Knoking ta yi ta kama abin ta bude ta shigewarta da salama da kuma sakin fuska sosai ta karasa wajen office din ta ajiye masa abincin da katinsa tana kallonsa ta ce" Hajiar fa ta sauka kana office TAUFEEK ka sauko ka ga baby girl mai kyau da ita Masha Allah" Yi ya yi kamar bai ji mai take fada ba yana ta rubuce rubuce a baban litafin dake gabansa Dan dage ta yi ta ga aiki ne yake sosai, dan haka ta ajiye ta masa salama ta fice Sai da ta fita ya dakatar da rubutun da yake yi a hankali ya jinginar da bayansa jikin kujerar nan ya lumshe idannuwansa Tabbas ya san bashi da lafiya, zai kirayi docter ta dauki jinninsa may be rashin isashen hutu ne ke neman sakashi kwonciya Khausar na tare da ahalin gidan mai kwanoni har aka salame su daga asibiti Mota uku suka cika har ita suka nufi gidan domin dangin Hajiar sun fara halarta summa ta ko'ina, baby dai gata dangi na maraba da ita ama jikin uwarta du ya yi sanyi tamkar ba karuwa ta samu daga Ubangijin talikai ba wanda shi ya isa fitar da na kirki tsakanin mace da namiji, yana iya baka namijin ya zamo baban tashin hankalinka duniya ya kuma kaika wuta gobe kiyama, yana iya baka macen ta zamo itace jin dadinka mai jin kanka duniya da kiyama, har ta manta karin maganar da a haifi gwama gwara a haifi matar gwamna, ta gagije ta hade rai ko magana da kyar take yi, uwa uba abinda ta so bai samu ba cewa sai dai kishiyoyi su ga ta haihu, haihuwa mai dadi sai da ta tara mata kaf kishiyoyin ya zamo sunne suka kaita asibitin mijin yana gida yana hutawa dan ba dan fari kuma dan da bai taba samu za'a kawo masa duniya ba, ya zamana itace a ragaya itace a mumunan halin da ta saka zuciyyarta dan jin dadi, kamar zata mutu haka take ji saima idan ta bi Mama da kallo ta ga yadda take car car da ita kamar wace bata girmeta ba, dan kuwa ba zaka ce ta haifi taufeek ba, haihuwa daya haihuwar ta tsaya sai gayu da kanshi ke fita du inda ta tsaya tana walwali ita ga uwar dan masu gida ko?, Ba zaka taba cewa ta girmeta nesa ba kusa ba dan kuwa ita HAJIA yarinya ce haihuwar nan itace ta fari amarya take a gidan mai kwanoni cike da burika nata na kanta masu zaman kansu, sai fatan Allah ya bata Sa'a Sai da suka gama ajiye mata kayayakinta sannan suka wuce bangaren Hajia, Hajiar cike da mamakin Yumnah ko a leke ko kafarta ba'a gani ba a yanzunma ? Uhum.... Fira suka sha , KHausar cike da jin kunya domin HAJIA gyara zama ta yi ta saka Mama a gaba wai du abinda ya dace na yi a rubuta masu su fara zuwa kasuwa, ita saima da ta sha mamakin Kennan dai maganar aurenta dai da gaske ne? Mahaifinta yace mata da izinin ubangiji ya yanke aurenta nan da kwana goma, kai sai take ji wani iri, wai ita KHausar? Ashe dama mijin nata a bayan gidansu yake bata sani ba?, Allah mai hikima bata da abin fada sai hamdallah Bata tashi tafia gida ba sai da yama ta yi sosai domin har sai da ta haɗawa HAJIA yar tsala ta toya suka ci abinsu harda Mama sannan maman ta saka direba ya kaita har gida sai godiya take mata, HAJIA kuwa fadi take in sha Allahu gobe zasu je su ciro anko ita da TAUFEEK, ita kuwa daria kawai ta yi abinta tana tunanin HAJIA da rigima ina ita ina tisa Taufeek cirar anko? Cap itafa tunda ta san waye shi take wani kiyaye wasu abubuwan da a da kai tsaye take masa Koda ta huta sosai wayarsa ta gwada kira dan ta sanar masa da kanta domin ta san in HAJIA ta ji yanzu zai ji, ita kuma haka kawai bata so ya ji daga bakin wani, tana so ta ji irin murnar da zai yi, tana matukar so ta ji irin farin cikin da zai nuna , hakan nema ya sa har ta kusa shiga barci tana neman layinsa , sai dai cikin ikon Allah Sweet off ake fada mata, karshe dai haka ta hakura ta nemi na Salis , sai dai shi kuma tana ta ringin har ta katse bai daga ba , a dole ta yi kwonciyarta da nufin gobe asabar in sha ALLAH tana da isashen lokacin hutu da gyaran jikinta da kuma neman wayar TAUFEEK din , Salis kuwa ta sani ne a yau din sai ya nemeta dan haka ta kashe wayar ko zata samu isasshen hutu dan ta san in dai ya ga miss call DINTA zai kirayeta ne ya tsareta da firar dare Wasa wasa lokaci matsowa yake yi, lokaci da wuyar zuwansa saka shi ne dama, haka kuma cikin ikon Allah Mama ce da kanta mahaifiyar TAUFEEK ta yi kiran KHAUSAR cewar ta dakata da zuwa wajen aiki har a daura auren nata wanda dududu abinda ya rage kwana uku ne kawai, sai take ji kamar fa wannan din da gaske zai tabbata ne A kulun zata tashi ne cikin tarin fargaba da tsoro da faduwar gaba, bale a yanzu wayarta da Salis ta rage sosai ya zamtoma itace zata yi kiransa kulun idan ya daga kamar wanda yake cikin ɓaci ko busy kulun yana da uzurin da zai gabatar mata da nuna mata zai tabota ya katse kiransa hakan ya sa zuciyyarta ke cikin tarin zulumi da tsoro har take tashi tsakiyar dare tana fadawa Allah take kuma daukan azumi kan koma menene ke damunsa Allah ya sa ba na daina aurenta bane tunda dai zuwansa da farko farko ba haka yake ba Ana saura kwana biyu Hajiya ta yi wani zuwanta gidan suka dinke da Mama a daka , sai da yama sosai ta juya gida da tarin kyaututtukan da suka saka KHausar fashewa da kuka cike da gannin kokarin mutanen ta ringa yi masu Adu'a da tunanin koda bayan aurenta ne rabasu zumunci da mutanen nan da ita ba zai taba katsewa ba, abinda ya karra daga mata hankali kwana biyu saura a daura mata aure ama bata da labarin Taufeek, ta yi kiran, ta bar msg ama shiru, ko yanzu ta tambayi HAJIA sai take ce mata aiki ne ya mukemuke shi dan suma rabonsu da shi a yi fira ta gwa da gwa har sun manta, sam basa samun lokacinsa , duda haka dai ta so ta sake damun kanta da tunanin duba da bai taba share sati cirrr bai zo gidan nan ba, ama gashi har yau kwana takwas ba shi ba labarinsa? Gashi an kusa fara tafia HAJI , ta yiwuma har ya tafi bata da labari Da dare bayan Aba ya dawo da auta an dan taba fira Aban ke sanar mata wani sabon cenji cewar ba zata dauki dogon lokaci zata tare ba wai mahaifin mijin nata ya nemi alfarmar ta tafi gidanta da wuri , wannan ya sakata shiga hali irin na kimtsatsun amare, ba irin amarenmu na zamani ba da za'a masu auren sai dai su maka kiba su yi bulbul da su, maimakun su ringa zugewa saboda zulumin rabuwa da iyaye da tunanin sabuwar rayuwar da za'a je a tarar a gidan mijin, wanda in dai yarinya budurwar take dole tana cikin zulumin abubuwa da yawa masu firgita zuciyyarta Tarin fargaba da tsoro ya sakata da safe neman izinin zuwa gidan yan uwanta, wanda tunda aka yi auren kannen nata bata taɓa zuwa gidajensu ba dan kuwa takan ce in dai ba halin rashin lafiya ba ita din bana ce na zata je gotai gotai yin komai gidansu ba, sai dai su su zo gida lokaci zuwa lokaci dan su dinma Aba ya Hanna zuwansu koda yaushe yace su yi zamansu a dakunnansu su yi ibada Mama ta hanna mata tafiyar, karshema ta sakata zaman dakin dole, domin a yau din baki Mama ta ringa samu yan anguwa ne da sako ya je masu ta wajen auta cewar daurin auren KHAUSAR din gobe da safe a masalacin anguwar, sai kuma daidaikun dangi dake nesa da sukan zo da nufin kwana A yau din du sai ta idasa firgicewa, Bama idan aka daga labule dan a ga wai barci take ne? Har Kannenta suka iso ta ringa binsu da kallo irin murnar da suke a ranta tana tunanin shin ina madafa ta rasa Salis din tun jiya ta rasa da wa zata zanta tarin tsoro da fargabar dake zuciyyarta har dare ya tsala sawaye suka dauke sai daidaikun da zasu kwana a gidan a dakin Mama hakan ya sa ta labe ta ringa kuka ko abinci ta kasa ci ta kasa motsin kirki du ta haukace burinta daya ne a yanzu ta samu wayar TAUFEEK, ama amsa daya ce wayarsa a kashe? Shin ina zata saka ranta da tashin hankalin nan?....... 💔💔💔💔❤‍🩹❤‍🩹💔💔💔💔 *DA CIWO A ZUCIYATA* 💔💔💔💔❤‍🩹❤‍🩹💔💔💔💔 _MALLAKIN_ *SAJIDA NIJAR* *FREE BOOK NE* 3️⃣8️⃣ *GARABASA, GARABASA, PROMOTION, PROMOTION DIN LITATAFAN MARUBUCIYAR A KAN FARASHI MAI SAUKI 1K, YAN NIJAR KUWA 1000 FRANCS CEFA* 1: Duk karyar kada 2: Yar mahaukaciya 3: Neman na kaina 4: Bani da zabi 5: Bak'a ce 6: Kutkale 7: Makauniya ce 8: Mage 9: Duk nisan jifa 10: Idan ka raina inda kake 11: Dutse 12: Alkalamin kadarata 13: Bani da zabi 14: Dakika Biyar 15:Wata kokowar 16: Aure yakin mata 17: Ni zan ladabi 18: Daga tafia daukar soja *Dukansu a kan farashi mai sauki, zaka saka dubu guda ne domin promotion ne nake yi, ka tuntubeni kan layina kamar haka +227 93 81 16 18, Sajida Nijar* Now *Da CIWO A ZUCIYATA* *Tallah, tallah, tallah* *SECRET DE LA FEMME DU MANGA* _Gidan Kamshi, Sirrin Manyan Mata, nesa tazo kusa,Amarya ,Uwar gida,Ango da mai gida Har ma da yan mata da samari shin kuna sane da cewa HAJIYA FUSAM ta shirya tsaf domin gwangwaje ku da turarakunta masu dankaran kamshi? Tare Kayan gyaram jiki na musamman ,wanda daga nesa kamshin ki kadai ya wadatar ya isar da sakon zuwanki waje,gidan ki kuwa sai ya zam abun kwatance wajen kamshi, kar na cika ku da surutu bara in fara zayyano su_ Farar Humura Bakar Humura Humura special, humura de bain Humura epicé Lait de nuit Parfums désodorisant Parfums rideau et dras Lait de nuit Alkam Kulakcam *Waɗannan kadan ne daga bangaren turaran ruwa* Gagab, sandal flex, Durot, durus, sandal fleur, tafarce, farce, sandal bangui, sandal, hypotonic sandal, al'ut, coktail creation VIP, Gajiji, Mankaji, turaran wutar labule da cafet, Aba malan, boulettes *Munada bangaren gyaran jiki kamar haka:* mai mai saka santsin jiki, mai mai kanshi, Kayan gyaran jiki mai saka fata ta yi santsi da laushi, kayan gyaran jiki mai saka fata ta yi fari, Sabulu mai saka fata ta yi haske, sabulu mai saka fata ta yi santsi, sabulu mai goge yanayin fata, mai wanda baya saka fari mai gyara fata Sayen na gari mai da kudi gida,sai an gwada akan san na kwarai💃💃 Hajiya Fusam na zaune a kasar Niger domin yin magana da ita kai tsaye tuntuɓi wannan number 97 82 44 94 *SECRET DE LA FEMME DU MANGA* Gidan Kamshi, Sirrin Manyan Mata💃💃💃💃💃 Karshe wayar HAJIA ta shiga kira, tana ji a ranta in dai yana gidan Hajiar zata bata shi, zata masa kuka ya sanar masa ya rarasheta ya kuma tayata da addu'ar Allah ya sa a yin in ALKHAIRI ne Kira na biyu Hajia dake falonta zaune shiru, TV a kashe, rediyo a kashe, hankalinta a kansa ta kori yar gidan HAJIA tunda ya shigo falon suka zauna sunna zaman kurumci ta yi tambayar shin a kawo abinci ya kyaleta ta yi tambayar bashi da lafiya ne? Ya kyaleta, a kwonce yake saman sabuwar kujerarta da aka cenza mata ko kwana biyar basu yi ba, idannuwansa lumshe, gashin girarsa sun karra yin lumbuk sun yi sidik a goshinsa, hakama na idamnuwansa, jan lebensa jajajir ya bushe sosai sai hasken fatarsa da ya karru ya yi fayau da shi yana kwoncen bai ce mata ci kanki ba, itama kuma a zaunen da take kunshi ne ta kunsa a kaffafuwanta ta saka Safa saboda gobe idan Allah ya tashemu lafiya karfe shiga zuwa bakwai tana gidan su KHausar ai dan haka take gama komanta da wuri danma ta jima bangaren Mama sunna shirye shiryen abubuwan yi a goben ita da ita, da tunima kunshin nata ai ya jima a kafarta Tana daga kiran ta Muryar ta gane mai kiran, ta saki wani murmuahi tana dan gyara zama ta ce" Amarya ce? Khausara ya gidan ya shirye shirye ? Ai Ni dinma abinda ya sa baki ganni ba yau din shirin nake, kin dai ganni nan an kusan kunshi , kuma so nake sai an daura mu wuce kasuwa da yan matan gidanku mu ciro bayanin ankon, har ina cewa MAGIDANCI kala biyar cir zan ciro mu wuni muna rakashewa ranar tarewar ko?" KHausar ta ja hanci da kyar tana sake boyewa a jikin katifarta muryarta a raunane ainun ta ce" HAJIA, ina yini? HAJIA wai ko dai TAUFEEK ya yi tafia ne?" HAJIA ta yi shiru, ta yi kiskirin tana sauraron yannayin na khausar din, kasa kasa ta ce" Waye wai Magidanci? Gaya a falona ai ya min jikaka a kujera, bara in baki shi " Daga haka HAJIA ta dafa ta mike ta kai ta kanga masa wayar dan kamar wanda ya yi barci tana fadin" Amarya ce amsata" Idamnuwansa ya bude a hankali ya sauke dubansa a fuskar Hajiar, idannuwansa sun yi jajajir hakama hannunsa ya dauki zafi sosai HAJIA ta dauke kanta daga fuskarsa tana jin kamar zuciyyarta na neman gazawa ta mike ta yi gaba dan sai ta ji kamar zuciyyarta zata gaza daukan yannayinsa Shashekar da take yi da jan hanci yake sauraro, da kyar ya iya budar bakinsa da har ya fara sabawa da shiru shirun da ya aura kasa kasa sosai ya ce" Are u crying?" Kamar jira KHausar take ta bude idannuwanta da kyar da suka mata nauyi ta fashe da kuka muryarta a kurya tana yi ba ji ba gani har shasheka take yi A hankali ya lumshe idannuwansa yana jin kamar ba kukan nan yake da bukatar ji a irin wannan lokacin ba, sai dai cikin ikon Allah tana daya daga cikin mutanen da suke da alfarma a duniyarsa, ko me take so takan yi kanta tsaye ne ba ruwanta, shi kuma yana iya dauka koda a wani irin lokaci ne, dan haka yana sauraronta har ta ringa jan numfashi da kyar kafin ya iya budar bakinsa ya ce" ke fa likita ce, kin san irin daga hankali haka bashi da kyau ko?" "TAUFEEK na maka laifi ne?" Ta yi gagawar tare numfashinsa Shiru ya yi dan bai san me zai ce mata ba, laifin me kuma ? KHausar ta dora da fadi " TAUFEEK wayarka a kashe, gaba dayama Ni ka cenza min, me na maka ne? Ka san halin da ake ciki kuwa? Ance wai gobe za'a daura min aure da Salis kuma ka ga Salis yana neman ya min irin abinda Mujaheed ya min ko?, TAUFEEK bayan wannan aure fa nima wai aure, TAUFEEK kuma ka ga in shima ya guje min fa? TAUFEEK bashi da matsala Salis ya nuna yana sona nima kuma ina sonsa fa, TAUFEEK ka ga tsoro nake ji, hankalina du a tashe yake, na rasa me zan yi tunani, in fa aka fasa????? TAUFEEK ka ga............. "KHausar Please........." Ya fada muryarsa a cen ciki yana dan son bude idannuwansa ama sun kasa buduwa Da wata Muryar da bai san yana da ita ba mai daci da kaushi sosai ya ce" In ya fasa aurenki sai me?, Ya dace ki daina daga min hankali haka, saboda shi ne zaki zauna kina kuka kamar an kashe ki?, Why a kulun burinki ki Hanna min kwonciyar hankali? KHausar! Idan ya fasa aurenki a gobe kina iya daukan matakin da kike so ok?, Ba zan rarasheki saboda wani ya ki aurenki ba, Ni kuma halin da nake ciki wa zai rarasheni? I'm tired KHausar, na gaji plz!" TAUFEEK ya karashe fada yana sauke amon muryarsa a hankali, sai kuma ya katse kiran ya ajiye wayar nan ya mayar da idannuwansa ya lumshe Kamar an tsikare shi ya bude su da dan sauri yana duban wayar Hannunsa ya mika ya dauki wayar a hankali ya shiga kiran layin nata Ya yi kira ya kai sau biyar kafin ta daga, har saima da ya nemi waje ya zauna sannan ta daga kiran, kuma tana dagawa alamun kukan take kawai yake ji A hankali ya furta" I'm sorry KHausar" KHausar da abin ya nemi girmamar tunaninta a hankali ta ce" Na tambayeka na maka laifi ne? Ka ki bani amsa, ama me yasa ka cenza min?" Kasa kasa sosai ya furta " Kukan ne bana so" KHausar ta ja numfashi tana sauraron Sa, cen ciki ta ce" Ama wa zan yiwa kukan bayan kai kadai nake yi ma?" Wani irin sarawa da kansa ya yi sai da ya ji kamar ya rotsa wayar da kasa Da kyar ya iya saisaita kansa a hankali ya ce" A yanzu, kina da wanda zaki yiwa kuka KHausar....nd ya saurareki dolensa, domin idan bai yi ba ba zan iya kyale shi ba, ki daina kukan haka kin ji? Zai zo za'a daura in sha Allah, nima zan zo gidan da safe, ko yanzu kike so na zo?" KHausar ta ringa sauke ajiyar zuciya, tana jin wata salama na ziyartar zuciyyarta A hankali ta ce" A'a, dare ya yi, da safen sasafe zaka zo ko?" TAUFEEK a hankali ya furta" In sha Allah " KHausar ta sauke numfashi ta ce" Sai goben, thank you besty am" "By" ya furta cen cikin makoshinsa sannan ya kashe kiran A hankali HAJIA ta ja baya ta koma dakinta ta saka ky ta haye gadonta tana dan kada kafarta ita dai bata san fitarsa ba dan bata san yaushe ya fitan ba Tunda safe ya wayi gari da mamakin Yumnah, domin Yumnah ce da kanta ta ciro masa wani danyen yadi irin jikaken yadin nan na manya da hula da takalmi da su agogo komai dai sannan sai wani irin annuri take saki wanda ya jima bai ga irinsa a fuskarta ba taba sake fadin Bara ya je bangaren su Mama ta masu a dawo lafiya, shi ya zatama zata je ne itama, sai kuma ya kade ya ci gaba da shan lipton dinsa hankalinsa a rarabe yana jin kamar ya koma ya kwonta sai dai Aba ya jaddada masa kar ya ya dawo nemansa bangarensa dan karfe tara za'a daura auren KHAUSAR Takwas Saura HAJIA ta dawo zuwanta na uku Kennan ta masa tsaye ta ce" Wai ina direbobin gidan nan ne? Ya haka ina so in je a yi yan share share da Ni in mata yan turare turare na baki da yan uba ama kana zaune ba zaka kiri ko waye ya kaini ba?" A hankali yake dubanta, ta sha sabon dimkinta Masha Allah da farin hijabinta ta rangada kwali da kunshinta sai sakin murmushi take fuskar nan kamar ita ta haifi KHausar farin ciki a bayyane yake wanda ya gaza gane na menene Ajiyar zuciya ya sauke a Nutse ya mike da nufin yi mata kiran direban, sai dai yana mikewar ya ji wani irin jiri yana neman maka shi da kassss Har sai da ya daki jikinsa da jikin table din ya dafe garu da karfi sannan ya iya rike kansa Lokaci daya Hajiya ta nufo shi tana neman taro shi bakinta kuwa ta buda ta shiga ihun a taimaketa Magidanci zai summa A hankali ya zuba mata ido kasa kasa ya ce" Ni na fada maki zan summa?" HAJIA ta yi tsuru tana kallonsa, sai kuma ta ce" Au, na ga ne kanna lumtu kamar zaka dauke" A hankalin dai ya ce" Cikani" HAJIA ta ga ashe daurin agogo ta masa, dan haka ta cikashin tana ankarewa kar ya ruftu a kasa ya sakata uku kamar wata wace zata iya rike shi Baya baya ta yi tana fadin" Ka ga kama yi zamanka kawai bari mu mu yi gaba da mai kwanonin tunda shima na ga ya fito tun dazun dan ya tara baki sosai" Da mamakin furucinta ya rakata da ido har ta shige sannan ya shiga takawa a Nutse ya nufi sama dan kimtsawa domin ba zai yi wasan abansa ya sake tuntubarsa ba, sai dai mamakin dangin nasa ya gama cika shi, lalle KHausar ta zama ahalin gidansu Kennan har gaya Aban ya yi shi bai sani ba? A yau take babar rana💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻AUREN KHAUSARA DA SALIHU DAN KIRKI💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻 Biki namu ne Wata aunty tace zata dauki nauyin rubutun nan baki dayansa, yaya kuka ce al'uma? 😍😍😍😍😍 💔💔💔💔❤‍🩹❤‍🩹💔💔💔💔 *DA CIWO A ZUCIYATA* 💔💔💔💔❤‍🩹❤‍🩹💔💔💔💔 _MALLAKIN_ *SAJIDA NIJAR* *FREE BOOK NE* 3️⃣9️⃣ *GARABASA, GARABASA, PROMOTION, PROMOTION DIN LITATAFAN MARUBUCIYAR A KAN FARASHI MAI SAUKI 1K, YAN NIJAR KUWA 1000 FRANCS CEFA* 1: Duk karyar kada 2: Yar mahaukaciya 3: Neman na kaina 4: Bani da zabi 5: Bak'a ce 6: Kutkale 7: Makauniya ce 8: Mage 9: Duk nisan jifa 10: Idan ka raina inda kake 11: Dutse 12: Alkalamin kadarata 13: Bani da zabi 14: Dakika Biyar 15:Wata kokowar 16: Aure yakin mata 17: Ni zan ladabi 18: Daga tafia daukar soja *Dukansu a kan farashi mai sauki, zaka saka dubu guda ne domin promotion ne nake yi, ka tuntubeni kan layina kamar haka +227 93 81 16 18, Sajida Nijar* Now *Da CIWO A ZUCIYATA* *Tallah, tallah, tallah* *SECRET DE LA FEMME DU MANGA* _Gidan Kamshi, Sirrin Manyan Mata, nesa tazo kusa,Amarya ,Uwar gida,Ango da mai gida Har ma da yan mata da samari shin kuna sane da cewa HAJIYA FUSAM ta shirya tsaf domin gwangwaje ku da turarakunta masu dankaran kamshi? Tare Kayan gyaram jiki na musamman ,wanda daga nesa kamshin ki kadai ya wadatar ya isar da sakon zuwanki waje,gidan ki kuwa sai ya zam abun kwatance wajen kamshi, kar na cika ku da surutu bara in fara zayyano su_ Farar Humura Bakar Humura Humura special, humura de bain Humura epicé Lait de nuit Parfums désodorisant Parfums rideau et dras Lait de nuit Alkam Kulakcam *Waɗannan kadan ne daga bangaren turaran ruwa* Gagab, sandal flex, Durot, durus, sandal fleur, tafarce, farce, sandal bangui, sandal, hypotonic sandal, al'ut, coktail creation VIP, Gajiji, Mankaji, turaran wutar labule da cafet, Aba malan, boulettes *Munada bangaren gyaran jiki kamar haka:* mai mai saka santsin jiki, mai mai kanshi, Kayan gyaran jiki mai saka fata ta yi santsi da laushi, kayan gyaran jiki mai saka fata ta yi fari, Sabulu mai saka fata ta yi haske, sabulu mai saka fata ta yi santsi, sabulu mai goge yanayin fata, mai wanda baya saka fari mai gyara fata Sayen na gari mai da kudi gida,sai an gwada akan san na kwarai💃💃 Hajiya Fusam na zaune a kasar Niger domin yin magana da ita kai tsaye tuntuɓi wannan number 97 82 44 94 *SECRET DE LA FEMME DU MANGA* Gidan Kamshi, Sirrin Manyan Mata💃💃💃💃💃 Sai dai me, hawansa saman ya samu ya yi wankan, ama yana fitowa daure da tawul ya kai zaune bakin bed dinsa a hankali ya zubawa Katinsa ta shedar waye shi ido Katin ya mika hannu ya dauko ya sake zuba mata ido A hankali ya ringa jin wani yannayi da bai taba ji a duniyarsa dangane da aikinsa ba irin na yau Tarin jin kiyayar aikin a cen cikin zuciyarsa ya ringa ji abin na ruruwar masa har kamar idannuwansa zasu rufe Hucin takaici ya sake fitarwa a hankali ya ajiye katin a inda ya dauke shi ya shiga tunanin shin me kuma *AIKINSA DA HUKUNCE HUKUNCEN AIKIN* zasu saka ya rasa?, Anya zai taba rashi irin wannan kuwa? Mikewa ya yi da kyar ya karasa ya bude wajen tufafinsa ya ciro wasu, domin a suturar da Yumnah ta fitar masa bai ga zai iya anfani da su a ranar nan ba, Sakawa ya yi ya gama yana dan anfani da turare Yumnah ta nemi izinin shigowa Bai bata dama ba sai karasowa da ya yi ya bude ya sauke mata kaifafun idannuwansa a saman fuskarta Sosai ta ji gabanta na faduwa gannin yannayinsa Muryarta a matukar sanyaye ta ce" Au, baka tafi da su Aba ba? Na zata tare kuka fita tun dazun" Irin yadda farin cikinta ya kasa boyuwa har mamaki abin ke bashi A nutsensa ya ce" Kin kagauta na tafi ne Yumnah?" Da sauri ta kalli fuskarsa, sai kuma ta wayance ta ce" A'a, gani na yi aminiyarka ce, irin yadda kuke tare ya dace ace kana cen din da wuri Yayanmu" Murmushi ya saki a hankali ya ce" Yanzu zan tafi" Itama murmushin ta saki, sai dai gannin yana nan din ta daina tafiya dakin nasa ta juya da dabara ta koma nata bangaren, waya take da mahaifiyarta tamkar zasu taka rawa ta wayyar, gaba daya yan ciwace ciwacen da ta fara ji na cikin yau din bata jinsu, tunda ta je bangaren cen HAJIA ta sanar mata yau fa mijinta ke aurar da aminiyarsa ta ringa farin ciki ta jita wasai ya zamo a yanzu kaam duniya bata da wata damuwa , ko Meye zai zo ya zo bata da wata damuwar kuma, harma kyauta zata yiwa wannan mata irin na gyaran gida, a je cen a karata a bi wani sarkin, nata dai kam ya kubuta, tana mata fatan mutu ka raba ita fa mijinta, sai dai ko nan da nan ba zata je ba, ba ruwanta da ba kai wahala a banza a wofi, hatta bangaren su HAJIA yau ba zata leka ba dan kuwa ba zata je gayar sodi ba, har mamaki Maman TAUFEEK ke bata, lalle sa gaskiyar HAJIA kishiyarta matar ta cika ba kai wahala da neman waje wajen d'anta kamar shine uwar ita Yar! Ba ruwanta da aikin bata lokaci gaskiya TAUFEEK na nan yana bata lokaci bai sauko din ba Wayarsa ta dauki kuka Karasawa ya yi wajen wayar ya dauka yana dubawa Gannin sunnan mahaifinsa sai da ya ji tsam a ransa dan ya tabbata fada ne Aba zai yi na bai fito sun tafi tare ba, gashi yanzu har sha daya ce fa zata yi, shi karyawama bai yi ba ya dai sha bakin tea "Wa alaika Salam wa rahamatulah" Aba ya amsa salamarsa a Nutse kafin ya budi bakinsa da kula ya ce" Tunda baka samu halartar daurin aurenta ba, ka yi kokari ka kasance cikin masu tayata farin ciki da addu'a, an daura auren KHAUSAR yanzu" Wata irin zufa ce ta karyowa TAUFEEK lokaci daya hadi da faduwar gaba da bugawar zuciya Sama sama ya idasa tsintar maganar Aba da kashewar wayar Aba sai idasawa da ya yi saman gadonsa a hankali yana rike da gaban goshinsa ya sadada jikinsa na idasa cire dukkan wani launi da kuzari da wani karfi karfi tasss ya bar jikinsa kafin idannuwansa su masa nauyi ya idasa kule su a hankali yana ambaton sunnayen Allah a cen kasan zuciyarsa A irin wannan lokacin da TAUFEEK ke wannan bidiri, a irin lokacin ne Kannenta suka fuskanceta dan sanar mata asalin abinda yake faruwa a duniyarta wace take bakuwa a gareta , boyayiwa a gareta, gigitaciya, firgitaciya sannan wace zuciya ba zata taba dauka a wajenta ba Kallonsu take yi irin kallon nan na bakinta ne su din a duniyarta Hawayen da A'isha ke yi take bi da kallo kafin ta kalli fuskar Rukaya Kai ta cire tana jan dan tsaki saboda gannin wani salamamen rainin hankali daga kannen nata a yau din da take ranar aurenta Wayarta dake gefe ta sake laluba a Nutse ta kuma buga kiran numbar Salisss, ama amsa daya ce sweet off Dubanta ta kai wajen A'isha dake mamakin yannayinta da irin yadda ta nuna kamar Wada bata yarda da furucinsu ba, ta ce" Ke dan bani wayarki na gani, rabona da Salis yau kwana uku Kennan , abin ya fara damuna" Mamaki mai tsanani ya saka yan matan dubanta a zabure sannan suka kalli junna, ga yar hayaniyar HAJIA da daidaikun bakin gidansu dake ta kai kawo a tsakar gidan dan kuwa ba wani cika jama'a aka yi ba, Hajiar kanta tun zuwanta bakinta bai yi shiru ba, ta yi nan ta yi cen ne cikin irin nata shiri da ta zo da shi, haƙoranta a fili kamar an mata albishir da gidan aljanna A'isha ta ce" Aunty , me hadinki da wani cen shashasha kuma ana maki magana ta namiji har namiji Yayanmu a yau Adu'armu ta karbu burinmu ya cika?" A harzuke , jin maganar rainin dai A'isha zata ci gaba da mata ta dafa ta mike lokaci daya zannin da ta daura saman doguwar rigar barcinta irin mai santsin nan har kasa wace ta kasa cenzawa tunda ta yi wanka sai zani kawai ta dora Mata a samanta ta zurma hijab take jiran zuwan TAUFEEK ko ya fita ya gano mata me ya samu Salis ya kwonce ta kuma ki bi ta kansa ta cire hijabin dan jin wani zafi ya fara ratsa mata jiki da fata ta bude yan yatsunta ta nufi fuskar A'isha zuciya daya muradi daya shine ta saukewa A'isha gigitacen marin da zai sa ta gane me take fada ko zata saita harshenta ta mata magana da Yaren da ta iya ba sakaran Yare ba, sai dai gannin haka da gudu Aishar ta yi bayan Hajia da ta shigo fuskar nan kamar gonar auduga tana salalami da fadin" Aunty dukana zaki yi?" KHausar rai bace ta ce" Idan ban dauke ki da mari ba ki ce min shashasha, sa'arki ce Ni wai? Ni zaki rainawa wayo ne?" HAJIA da ta ta yi dibi dibi sakamakon cakumeta da A'isha ta yi dan neman agaji ta yi raf da hannun A'isha ta ce" Ke tsaya ta mareke, in dai rainawa matar MAGIDANCI wayo zaki yi tsaf zan daureki mu zane banza, aikin banza ya zaki saka ta kunce zani tana tiitirniya ki tara mata gajiya? Ke dauko zanninki daura Ni ga galan din cen maza kafin nan zuwa dare shanye min shi tass, yanzun wancen gidan zan je in ga ubanda ya Hanna mattar mai kwanoni zuwa daurin auren MAGANIN gida magajin dukiya alwalin Gawa, dan daura kar a shigo a tsaya kallo wannan sababi hakka Masha Allah " KHausar ta yi kasakai tana kallon HAJIA, bayanan hajiar na son rikitar da tunaninta fiye da na su Rukaya A hankali Rukaya ta zagaya ta ja mayafinta ta nufi dakin mamansu a lokacin da Khausar ta matso daf da HAJIA ta ce" HAJIA, wai an daura auren ne? Da Salisss ko?" HAJIA dake rike da hannun A'isha taf ta sakarwa KHausar harara da jin haushi ta ce" Uban wanene SALIHU kuma ke Khausara? Ki fa kiyayeni yaya ina baki kina roko?, Maganar Magidanci zaki hada da wani shashasha?, Ke amshi nan, nace amshi uwaki, to wa bilahilazi sai in zaneki tas bayan Mamuda ya rike min ke, to ke matar MAGIDANCI kike ba SALIHU ba!" HAJIA bata san cewa ita ke dauke da kalaman fadi, KHausar ke dauke da abin aikatawa A birkice KHausar ta zaro ido, lokaci daya jikinta ya dauki rawa Ƙasa ta silale daidai shigowar Mama dakin da salama a bakinta KHausar na hada zufa kamar da wasa lokaci daya ta yi wani wiki wiki da ita ta dubi mama muryarta cen ciki ta ce" Mama, kin ji abinda HAJIA ke fada da Yaren nan kuwa? Yanzu fisabililahi wannan maganar a tsakani mutun da ita ce? Innalilahi ina Ni ina TAUFEEK zasu ringa min wani magana daban? TAUFEEK ai haramunane dan uwana ne fa" HAJIA ta zarro ido lokaci daya ta rike baki ta ce" To fa, yau ga zamanin yan iska!" "Mama ina Ni ina Besty? Aure? Aure dai aure? Shi auren nan dai aure? Haba Mama fisabililahi idan Salisss dinma ya fasa sai kawai a ba TAUFEEK? Na nawa nema taufeek din ina maganar aure Ni da shi? Aure mama aure? Innalilahi ai ba maganar soyayya bale zaman aure tsakanina da shi ko?" HAJIA kam ta gaza rike salamamen rashin mutuncin nan ta gyara zaman sabon hijabinta ta riko hannun Mama dake tsaye itama baki bude tana kallon yadda KHausar ke bayani baki bude dan kuwa sai malolowa take yi kamar mai fama da zazafan ciwon ciki ta mirgina nan hannunta a mike tana bayani hawaye wani na korar wani ga kan nan ta kunce shi baima samu gyaran saloon din ba nunawa kawai take tana hawaye ta ce" Kin ga, bari in tare bakin cen dan ba'a rasa yan munafurcin da basa son tarayar nan ba, ita kuma wannan y'a ki san ta inda zaki biyo da ita dan wa bilahilazi a kan auren nan sai in batawa kowa, rainin hankali za'a min? Me take nufi da yaushe aka haifi Magidanci? Allah kawo ki dakinsa sai mu sake zaunawa, dama da wahala dan fari ka ganshi rass da wayo abinsa, ke dai Allah shirya kuma in bata shanye tsumin nan ba na dawo nice nan zan mata wankan rubutu in sauke mata aljannun kanta!" Cabdijan, watau yar kukutar Aba fa so take ta kankaro mana rikici na kasa da kasa, baki san ainahin waye shi ba yarinya mu karki janyo mana, Meyema to in ba neman rigima ba, bakin cikin cinya sa zaki mana kau? Ta Allah ba taki ba wai SALIHU 🙄🙄🙄 .💔💔💔💔❤‍🩹❤‍🩹💔💔💔💔 *DA CIWO A ZUCIYATA* 💔💔💔💔❤‍🩹❤‍🩹💔💔💔💔 _MALLAKIN_ *SAJIDA NIJAR* *FREE BOOK NE* 4️⃣0️⃣ *GARABASA, GARABASA, PROMOTION, PROMOTION DIN LITATAFAN MARUBUCIYAR A KAN FARASHI MAI SAUKI 1K, YAN NIJAR KUWA 1000 FRANCS CEFA* 1: Duk karyar kada 2: Yar mahaukaciya 3: Neman na kaina 4: Bani da zabi 5: Bak'a ce 6: Kutkale 7: Makauniya ce 8: Mage 9: Duk nisan jifa 10: Idan ka raina inda kake 11: Dutse 12: Alkalamin kadarata 13: Bani da zabi 14: Dakika Biyar 15:Wata kokowar 16: Aure yakin mata 17: Ni zan ladabi 18: Daga tafia daukar soja *Dukansu a kan farashi mai sauki, zaka saka dubu guda ne domin promotion ne nake yi, ka tuntubeni kan layina kamar haka +227 93 81 16 18, Sajida Nijar* Now *Da CIWO A ZUCIYATA* *Tallah, tallah, tallah* *SECRET DE LA FEMME DU MANGA* _Gidan Kamshi, Sirrin Manyan Mata, nesa tazo kusa,Amarya ,Uwar gida,Ango da mai gida Har ma da yan mata da samari shin kuna sane da cewa HAJIYA FUSAM ta shirya tsaf domin gwangwaje ku da turarakunta masu dankaran kamshi? Tare Kayan gyaram jiki na musamman ,wanda daga nesa kamshin ki kadai ya wadatar ya isar da sakon zuwanki waje,gidan ki kuwa sai ya zam abun kwatance wajen kamshi, kar na cika ku da surutu bara in fara zayyano su_ Farar Humura Bakar Humura Humura special, humura de bain Humura epicé Lait de nuit Parfums désodorisant Parfums rideau et dras Lait de nuit Alkam Kulakcam *Waɗannan kadan ne daga bangaren turaran ruwa* Gagab, sandal flex, Durot, durus, sandal fleur, tafarce, farce, sandal bangui, sandal, hypotonic sandal, al'ut, coktail creation VIP, Gajiji, Mankaji, turaran wutar labule da cafet, Aba malan, boulettes *Munada bangaren gyaran jiki kamar haka:* mai mai saka santsin jiki, mai mai kanshi, Kayan gyaran jiki mai saka fata ta yi santsi da laushi, kayan gyaran jiki mai saka fata ta yi fari, Sabulu mai saka fata ta yi haske, sabulu mai saka fata ta yi santsi, sabulu mai goge yanayin fata, mai wanda baya saka fari mai gyara fata Sayen na gari mai da kudi gida,sai an gwada akan san na kwarai💃💃 Hajiya Fusam na zaune a kasar Niger domin yin magana da ita kai tsaye tuntuɓi wannan number 97 82 44 94 *SECRET DE LA FEMME DU MANGA* Gidan Kamshi, Sirrin Manyan Mata💃💃💃💃💃 HAJIA ke cikin fada, bata ankara ba Mama ta kaiwa bakin KHausar bugu tana hade girar sama da ta kasa "Lah ha ila ha ilalahu Muhammadu rasululahi sallalahu alaihi wa Salam, ke me ta maki?" HAJIA ta fada tana tarewa dan Mama abin haushi ya bata yadda KHausar ko kara babu take abu kamar wace ta. Samu tabin hankali, yanzu ta budi baki ita KHausar ta ringa rufi irin wannan? Lalle dan Adam, nan KHausar ke fadin ko waye aka bata tana so, itama burinta ace an mata aure, shine dan wulakanci Allah ya amshi adu'arta yau din itama ta samu yanci irin na mata ama take wani abu kamar an ce an hadata aure da makiyinta? HAJIA rai bace ta ce" Kul , banda duka, daga fadin nusar da ita da baki da wayo?" Mama ta sada kanta tana ji ranta na ɓaci ta ce" HAJIA, KHausar fa wani sa'in zuma ce sai da wuta, in ba rashin hankali ba mu sa'anninta ne zata sakamu a gaba da kukan rashin godiyar Allah?, To ta kireshi shi marainin nata ta fada masa !" Daga haka Mama ta yi gaba ranta a bace HAJIA ta sakarwa A'isha harara ta ce" to ai sai ki bita, ga dukkan alamu in aka bar maku ita tsaf zaku sa kumarinta ya rage, bita bi mamanki kar na rama a kanki" A'isha ta yi murmushi ta juya ta fice, tana ji a ranta tunda take bata taba jin tsohuwar nan a rai ba irin na yau, lalle matar nan ALKHAIRI ce ita, kuma tana mata Adu'ar gamawa da duniya lafiya, wani gefe na cikin zuciyar Tata kuwa tarin mamakin yannayin auntyn nasu ya gama rike mata wuya, yanzu wace mace ce zata ki yayansu? Menene dalilinta na nuna kiyawarta a lamarin? Allah shi kyauta "Kin ga, ki rufawa kanki asiri da koke koke, tunda kin ga auren nan dai an daura shi ba kuma za'a kwonce ba da izinin mai sama, kar dan zuwan da zan yi in dawo ta shigo ta dakeki a banza a wofi kin ji? Ba dai Magidancin bane bai maki ba? Ai shan koko bukatar rai ba sai kin daga hankali ba idan ya ji da shi aka daura auren ki rintse ido ki masa jan ido ki ce takardarki, da bakinki sa komai? Yanzu ki daina wani kuka dan bashi da anfani kin ji y'ar albarka?" HAJIA ta fada bayan ta rike hannun KHausar ta tausasa muryarta ainun KHausar a hankali ta ce" HAJIA, Kennan shima bai san da wannan abin ba?" HAJIA cikin hikima Tata ta amsata da" Eh, bai sani ba, hasalima iyayenku suka tsayar da hakan bisa rokon mahaifinsa " KHausar cike da mamaki da wani firgicin ta ce" HAJIA aba na cen gidan ne ya nemi auren?" HAJIA ya ce" Eh, shi da kansa mai kwanoni ba" KHausar ta shiga gyada kai cike da kalar tausayi ta ce" Na san bai san inada saurayi ba, Ama HAJIA shima TAUFEEK din ai an cuta masa, auren dole ai akai masa shi dinma ko?" HAJIA ta gyada kai ta ce" Wannan haka yake, Ni Bama abinda zai batan rai a zo ana fadin kuma daga aurenki an sake ki y'ar nan, ke dai yanzu ki share hawayen ki ki tausayawa kanki, komai dan a bi a hankali ne, duniyar nan akoy mai gudun bacin ranki irin Magidanci? Idan kuka zauna sai ku yanke abinda ya dace da ku ko?" KHausar ta ringa jan hanci tana sauraron yar hayaniya bayan fitar Hajiya Gaba daya abin yana nema ya girmami tunaninta Ta rasa a inda zata ajiye wannan sabon abin Abu daya ta sani shine ita da TAUFEEK *HARAMUN DIN JUNNA NE*!, idan ta tuna menene aure da tsarabe tsarabensa sai ta ji hankalinta na neman sake tashi , da sauri ta ringa kade tunanin tana jin tamkar wace ta tafka sabo tuna abinma a ranta, 'Hum, Allah ya kiyashemu abin kunyar nan ba da mu ba, bawan Allah in ya ji wannan aiki ta yiwu saima ya yi kukan takaici!' ta ayyana a zuciyyarta ta kuma dauri zaman daki ba tare da ta fito ko ta kimtsa gashin kanta ba, ita bata ga lokacin ba wani abu wai shi gashi ba a yanzun kam, ana ta Kai wa yake ta kafa? Murmushi kawai HAJIA ke yi a ranta tana Ayana ' Tirkashi, ai Inaga Bama sai na wani boye masa ba, tunda har Allah ya yi yarinyarma ba zata amshi abin da dadin rai ba koda ta amsa din, ama ba Ni zan sanar maka ba zan bar mahaifinka ya sanar maka, abinda na sani daya ne tak a yanzu ka yi aure, a yanzu ka auri yar mutuncin da ta san darajar iyayenka, babu ruwana da kyan banza da farin fatar banza da iyayi na gayu, abinda na sani shine wannan yarinya itace daidai da kai, kuma bi izinillah itace haske a cikin hasken gidan Mai kwanoni!' A baban gida shagali ake yi wanda ya daure kan daidaiku daga cikin ahalin gidan, domin babu abinda ya fi basu mamaki da daure masu kai irin yadda suka ga Mama na shige da fice cikin fara'a da farin cikin da suka gaza hade mahadar abin, to su basu ga hadi ba, inma zaman bikin karar kawar danta ta yi niyar yi ta je gidan su yarinyar su yi zaman mana? Ta yi zamanta a nan harda girki da samun baki? Lalle, wani shagalin sai a gidan mai kwanoni! Gefe guda kuwa ga Hajia tana nata itama shagalin, dan kuwa ita din tuya ake ta yi ta masa ana fitarwa sadaka sosai , dan hakan ta shirya wunin yau din dama, sai da yama ta yi sosai ta kimtsa ta nufi bangaren TAUFEEK, domin ta tambayi yan matasan dake zuwa wajensa inda yake sun tabbatar mata yau din bai fito ba, sai kuma ta karra tabatarta a wajen mai gadi dan haka ta mike ta nufi bangaren nasa hankali kwonce Kamar yadda ta saba bayan sun gaisa da Yumnah ta sanar mata ta sanar masa itace, ama bayan zamanta a kalla ta dauki minti ya fi Ashirin bai sauko ba, hakan ya sa ta rasa shin hawa zata yi ko dai zaman zata ci gaba da yi ko Allah zai sa ya sauko? Gashi Yumnahma tunda ta hau bata dawo ba shiru kake ji Har HAJIA zata yi tafiyarta gannin shirun ya yi yawa ta tuna waye jikanta, idanma dodo yake a wani wajen banda a gareta da ahalinsa baki daya, ta tabbata in dai ya san da zuwanta ba zai dauki lokaci kalau haka bai sauko ba, dan haka ta juya jiki ba karfi ta shiga hawa tana salama dan gudun shiga hakin kowa A kofar dakin ta dakata ta yi bugu ya fi a irga tana Salama, ama yarinyar nan da dakinta ke daf da nasa bata fito ta nuna mata ta san da mutun a wajen ba, ita kuma ta ki ta hakura dan jikinta ke bata ba lafiya ba A bangaren Yumnah kuwa tana sauraron HAJIA, hasalima a tsaye take jikin kofarta tana murguda baki kasa kasa ta ce" Yau na ga jarabar naci, ba zan kira maki shi din ba, Ni kam Inaga bayan rabuwata da wancen a nacin saura wannan masifafiyar tsohuwar, a wuni sai ta mana shigowa uku in yana nan ta zo ta ishe shi da surutu ta tafi, ko mahaifiyarsa bata masa zuwan nan kamar yadda wannan mata ke yi, ba abinda ke bani haushi irin turare turaren shirmen da take masa, ko me take tunani?, Inma menene bata isa ta nunan son mijina ba ama sai tana abu kamar wace bata san me take yi ba, a barshi ya huta tunda bai fito ba ai damu ne baya so zan gani in har zaki shigo dakin kai tsaye ne, inama ace dakin na shige na same shi koda wani abin yake in dauki hankalinsa !" HAJIA kam jin shirun ya yi yawa ta shiga tunanin ko sauka take yi ta koma bangarenta ta yi kiran mahaifinsa ya mata kiransa ta ji yana kalau? Idan har ta ji an gama wannan ne kaɗai damuwarta dan bata son abinda take ji a ran nan nata Sai kuma ta shiga tunanin yaushe ta koma cen?, Kai ina , a dan daburce ta juyo ta kama kofar ta bude tana Salama da karfi hadi da Hanna idannuwanta dagawa koda taka tarda wani abin to fa ya zamto idannuwanta basu gani ba Shirun ya yi yawa, a hankali ta shiga bin dakin da kallo A gyare yake tsaf tsaf ga kanshin turare da sanyi mai karfin tsiya a ciki har idannuwanta suka sauka kansa wajen kujerar dakin ta gaf da gado kansa a saman kujerar yana zaune a kasa jikinsa ba riga dan ya samu ya cireta da ya raarafa ya yi sallar azahar daga ita bai samu yin ta la'asar ba domin yana kwatanta mikewa sai ya ji kamar za'a maka shi a kas ga wani ciwon kai mai tsanani da bugawar zuciyar da sam bai san zasu iya riskar shi a irin wannan lokacin ba Gaban HAJIA sai da ya fadi, ta dakata tana kiran sunansa ama ya kasa amsa mata Da sauri ta daga kaffarta ta karasa inda yake ta shiga tabashi da ambaton sunnansa A hankali ya iya buda idannuwansa ya sauke kwayarsu a saman fuskarta a lokacin da ta duko tana taba wuyansa ta ce" Subahanallah, Magidanci baka da lafiya ne dama ban sani ba? Ama dazun fa da na Barka kalau na tafi" Idannuwansa ya lumshe yana sauke numfashi a hankali yana lumshe sunansa kasa kasa , muryarsa cen ciki ya ce" HAJIA......, Kin dawo?" HAJIA ta gyada kai ta ce" Bari in kira a kaika asibiti kai fa baka iya ciwo ba, na shiga uku ka ga yadda idnanuwanka suka kade kuwa? Jiki du ya dime da zafi jijiya ta yi rado rado, kai subahanallah wannan yarinya da kake aure Ni tana da hankali kuwa? AI sai ki fada bashi da lafiya ko?" Da kyar ya iya karasa jin maganar da HAJIA ke yi, a hankali ya dan mirgina ya dora kansa saman kaffafuwanta dan hakan yake da bukata, shi dama mutun ne da bai iya ciwo ba sam, kuma idan yana ciwo ta yannayin shanyuwarsa ake ganewa ba zai zo da kansa yace ciwo yake ba har sai ciwon ya kayar da shi tamkar ba likita ba, HAJIA kam ji ta yi hankalinta ya kara tashi, domin ko yana ciwo bai cika yin laushi da ita haka ba, abinda tana ihun a kaishi asibiti yana fadan ba inda zai je? Ama yanzu jikinsa kamar ana rura wuta? Hankali tashe take janyo abin gadon dan hango salularsa da ta yi karamar , dan kuwa tana iya kamo lambar mai kwanoni da tasa tsaf a kanta Tana ta rubuta numbobin muryarsa cen ciki da kyar ya iya budar bakinsa a hankali ya ce" HAJIA, KHausar.....yanzu ta daina kukan ko? An mata auren ta huta ko?" Da sauri HAJIA ta yi cakkkkk daga abinda take yi tana kallonsa A raunane ta ce" Kai dai gaskiya bana so ma nace an ji kunyatu sai an saka nace, fisabililahi kar dai kace ciwon Kauna kake? To wai kai dilla mike🙄🙄🙄🙄🙄🙄🙄🙄 😨😨😨😨 Akoy fa rikici, watau ita Bama ta hango halal a ita da Magidanci ba, magidancinma nawa yake in ji matar jikan HAJIA!😨😨😨😨 💔💔💔💔❤‍🩹❤‍🩹💔💔💔💔 *DA CIWO A ZUCIYATA* 💔💔💔💔❤‍🩹❤‍🩹💔💔💔💔 _MALLAKIN_ *SAJIDA NIJAR* *FREE BOOK NE* 4️⃣1️⃣ *GARABASA, GARABASA, PROMOTION, PROMOTION DIN LITATAFAN MARUBUCIYAR A KAN FARASHI MAI SAUKI 1K, YAN NIJAR KUWA 1000 FRANCS CEFA* 1: Duk karyar kada 2: Yar mahaukaciya 3: Neman na kaina 4: Bani da zabi 5: Bak'a ce 6: Kutkale 7: Makauniya ce 8: Mage 9: Duk nisan jifa 10: Idan ka raina inda kake 11: Dutse 12: Alkalamin kadarata 13: Bani da zabi 14: Dakika Biyar 15:Wata kokowar 16: Aure yakin mata 17: Ni zan ladabi 18: Daga tafia daukar soja *Dukansu a kan farashi mai sauki, zaka saka dubu guda ne domin promotion ne nake yi, ka tuntubeni kan layina kamar haka +227 93 81 16 18, Sajida Nijar* Now *Da CIWO A ZUCIYATA* *Tallah, tallah, tallah* *SECRET DE LA FEMME DU MANGA* _Gidan Kamshi, Sirrin Manyan Mata, nesa tazo kusa,Amarya ,Uwar gida,Ango da mai gida Har ma da yan mata da samari shin kuna sane da cewa HAJIYA FUSAM ta shirya tsaf domin gwangwaje ku da turarakunta masu dankaran kamshi? Tare Kayan gyaram jiki na musamman ,wanda daga nesa kamshin ki kadai ya wadatar ya isar da sakon zuwanki waje,gidan ki kuwa sai ya zam abun kwatance wajen kamshi, kar na cika ku da surutu bara in fara zayyano su_ Farar Humura Bakar Humura Humura special, humura de bain Humura epicé Lait de nuit Parfums désodorisant Parfums rideau et dras Lait de nuit Alkam Kulakcam *Waɗannan kadan ne daga bangaren turaran ruwa* Gagab, sandal flex, Durot, durus, sandal fleur, tafarce, farce, sandal bangui, sandal, hypotonic sandal, al'ut, coktail creation VIP, Gajiji, Mankaji, turaran wutar labule da cafet, Aba malan, boulettes *Munada bangaren gyaran jiki kamar haka:* mai mai saka santsin jiki, mai mai kanshi, Kayan gyaran jiki mai saka fata ta yi santsi da laushi, kayan gyaran jiki mai saka fata ta yi fari, Sabulu mai saka fata ta yi haske, sabulu mai saka fata ta yi santsi, sabulu mai goge yanayin fata, mai wanda baya saka fari mai gyara fata Sayen na gari mai da kudi gida,sai an gwada akan san na kwarai💃💃 Hajiya Fusam na zaune a kasar Niger domin yin magana da ita kai tsaye tuntuɓi wannan number 97 82 44 94 *SECRET DE LA FEMME DU MANGA* Gidan Kamshi, Sirrin Manyan Mata💃💃💃💃💃 A raunane Hajia ta ce" Eh an daura ama tana cen tana ihun bata so kuma, y'ar nan dai sai addu'a sosai abin nata sai addu'a dan nan, gashi aure ya dauru kuma" Idannuwansa da sukai masa nauyi ya bude yana kallonta, ya dan dauki lokaci yana nazarin maganarta kafin ya ce" bata so? Auren da ta kawo mutumen da kanta ne bata so Hajia.......... ........." Ya karashe yana sake rintse idannuwansa da karfi saboda sara masa da kansa ya yi Hajia ta so cicidawa da shi ama ta gaza dan gaba daya yana son sage mata gwuiwoyinta da nauyinsa da kuma rigimarsa, da kula sosai ta ce" Eh wai bata so ina ita ina mijin , yaro ne meye meye, kai dai abu sak irin na kamun aljannu da kyar na fito dan na ji a raina kamar kana wani hali " Shiru yanzun ya mata, shiru sosai ya mata banza, ta ci gaba da maganarta ya kyaleta Jin ya yi shiru ya saka Hajia taba wuyansa, sosai jikinsa keda zafi haka kuma ita da ya ajiye kansa a saman kafafuwanta tana iya jin yadda zuciyarsa ke bugawa Da kula ta ce" Bari in kira mai kwanoni mu je a kaika asibiti magidanci ka ji?" Shiru ya mata bai ce mata eh ko a'a ba, shi kadai ya san irin nauyin da karfin da kansa ya masa, jikinsa kuwa tamkar ba nasa ba haka yake ji Hajia ta samu da kyar ta sauke kansa ta ɗora saman filo harda rufa masa abin rufa sannan ta fita ta sauko kasa tana faman duba wayarta Turus ta yi tana kallon Yumnah, wace ke zaune a baban falon kafa daya kan daya tana amsa waya, yannayinta na iya fasara maka halin farin cikin da take ciki, Itama Yumnar da mamaki take kallon Hajiar, domin a tunaninta Hajiar ta jima da barin gidan ai Bata ce mata komai ba ta yi hanyar fita sai sake riƙe hijabinta take yi, ita yanzun ai bata da lokacin uban kowa tunda magidanci ba lafia , bari dai a kaishi asibiti a dawo sai ta rikita kowa a gidan nan, ta kula yarinyar nan banda abinda ke damunta na rashin auki harda hauka take fama da shi, wannan ai ba matar auren magidanci bace, ace magidanci ba lafiya matarsa zaune tana waya? Sakarcin banza sai fama da kashi a wuya ita ga mace, shirme zata ga mata gannin idonta Karasawa ta yi har bangaren su Mama ta hadu da yarinyar wajen kishiyar maman wace take riko wato Hamdiya Wayar ta mika mata ba tare da ta iya amsa gaisuwarta ba ta ce" Ke Hamada dubo min lambar mai kwanoni kaina ya fashe na gaza ganewa dama Ni a duniya lambar magidanci kadai na hadace a kaina" Cike da ladabi Hamdiya ta amsa ta fitar da numbar aban ta aika kiran sannan ta ba Hajiar Hajia ta dakata har Aba ya daga wayar ta dan matsa tana rage murya ta ce" Kana ina ne Ni?" Aba ya sanar mata cewa yana tare da baki ne dan bai zaci yar gayar da ya yi za'a taru haka ba Hajia ta ce" To ko me kake yi ka bari ka zo ka kaimin magidanci asibiti, ka ganshi cen rai a hannun Allah jikinsa zafi rau, Ni abin ya bani tsoro tunda Ni din nan ya dora kansa a kafata yana min magana a sanyaye ka san kuwa ba lafiya ba dan in dai lafiyar Allah ai bama magana a hankali da Magidanci ko?" Aba ya yi dan tsai jin TAUFEEK ba lafiya, ga yadda Hajia ke kwatancen kamar sosai ne A tausashe, da ladabi irin na d'a da mahaifiyarsa Aba ya ce" Subahanallah, kin ga kuma lafiyar Allah na baro shi dazun, to ganinan zuwa sai mu gani in asibitin za'a kaishi Hajia" Hajia ta ce" Shine ai , ka ga magidanci ba hakurin ciwo ama wannan baba ne, kafin ka dawo bari in masa turare kar aje wani kafurin marar mutunci na son cinma jikana, sambatu daya yake yi bawan Allah, ama duda haka sai da ya yiwa Khausara fatan alkhairi , ina jiranka ka ji Elhaji baba?" Daga nan suka yi salama, Aba ya yi murmushi ya gyara zamansa ya ci gaba da kulawa da bakinsa dan kuwa cutar da akace Elhaji karami na yi bai sakata a ransa ba, bale ta dame shi Hajia ta kashe kiran suka yi ido hudu da Hamdiya dake tsaye yannayinta du wani iri Hamdiya murya a raunane ta ce" Hajia Yayan namu ne ba lafiya?" Hajia ta karra zuba mata ido, irin yadda idannuwanta suka cika da kwala sai da abin ya bata mamaki, a gidan nan tana iya cewa yadda take shiri da yarinyar ko da jikokinta sauran su Ishirat basa yi haka, domin yarinyar akoy hakuri da son shiga jikin Hajiar, du irin yadda marikiyarta ke hannata kulun tana gindin Hajiar Hajia ta dauke kanta ta ce" Eh shine, ama da sauki in sha Allah dan yanzu zan turara masa hantiti da kaka ka yi ka fito ba komai bane sharin masharanta ne!" Daga haka ta yi gaba, ita kuma Hamdiya ta nemi waje ta zauna hankalinta na neman tashi, sosai ta ji hankalinta na neman tashi, dan kuwa a jiyan nan Hajia Fatahiya ta yi wata magana a gabanta wace ta tsaya mata a rai ainun, kuma tana matukar tsoron ya zamto shirmen da matarsa ke yi a baibai ya zamo ila a gareshi, bata jin zata iya hakurin kawar da kai har wannan abu ya tabata, domin bata san girman laifin abin da irin inda zai kai ba, a da tana duban Yumnah da duba kala biyu, gagarumar wace ta shiga tsakaninta da abinda ya zamto buri, fata idan har allhairinta ne, sai kuma kallon wace ya zama wajibi ta girmamata dan ta zamo baba a cikin manyan gidan, daga baya da ta ga wacece Yumnah matar da Allah ya bata dama take wasa da ita, wace idan hanyar kirsar nema bata dauko ta kirki ba, tunda ta yi wasa da abinda mahaukaci kadai zai yi wasa da shi watau mahaifiyar mijinka ka dauketa abar gaba ko wata abar ka yi kishi da ita, sai ta fara saka ayar tambaya a kan hankalinta, a hankali ta ga take takenta a kan Hajia kaka , hakan ya karra tabatar mata da wahala idan akoy hankali a tare da kwakwaluwar Yumnar, sai ta yi watsi da duk wata girmamawar da take jin zata iya yi mata ta kuma daukarwa ranta abar gabarta ce kuma wace zata yi iya yinta dan gannin ta nuna mata ba haka ake rike namiji ba, koda sakaran namiji ne bale TAUFEEK MAI KWANONI, Kadara a cikin manyan kadarorin jinsin maza, bijimi kuma hamshaki a duniyar maza.... .. A hankali ta mike ta koma ta shige cikinsu ta kuma saki kunnayenta a firarsu, fira irin ta munafuntar junna da ha'intar junna a tsakaninsu, wace suke yi domin ta sun gaza gane ci gaba take samu a kowani kwana na duniya, sun gaza shafa mata lafiya su rayu hankali kwonce kamar yadda take rayuwarta , a gaban junna sunna nunawa junna kauna a bayan junna sunna ji kamar su kashe junna, a tsakaninsu ma sunna ha'intar junna, ta yi zaman nan ne kunnayenta na jiye mata ire irin zagin da suke sakarwa na habaici wa Mama, cewar dan kawai ana auren kawar danta ta baje harda su gaya kamar tana aurar da y'ar cikinta, sunna fadi cewa ana wasa da arzikin mijinsu ana takama ana gwaninta, Haka ta yi ta zama , zaman da take gannin bata lokaci ne domin ba wannan firar take son ji ba, maganar taba lafiyar Ƴaƴansu , uba a garesu sannan mafarkinta take son ganewa shin Hajiar ta aikata aikin ko bata aikata ba? Idan ta aikata lalle lalle zata je ta sanarwa Elhaji baba sai dai ko wace wace! Wasa farin girki in ji yan magana, karamin abu sai da ya girgiza Hajia domin komawar da ta so yi gidan su KHausar tana ji tana gani ta kasa , haka har dare ya yi tana bangaren TAUFEEK, a dole matarsa ta gane shi din ne ba lafia itama ta tare kusa da shi, ya zamto Mama abinci kawai take turo masu bayan hajiar ta yi kiranta tana fadan yau ita da mai kwanoni ne A gidan su TAUFEEK ake wannan lamari, a gidan su KHausar kuwa karshe sai da Mama ta samu Khausar din ta yi mata wankin baban bargo kafin ta tsagaita kukan da take yi, Maman ta fice ta barta a dakinta tare da yan uwanta har kusan magariba sunna tausarta Bayan sallar isha aka zo daukan Rukaya, cikin girmamawa da rarashi Rukayar ta sake sada kanta ta ce" Aunty, dan Allah ko menene ki fadawa Allah, Aunty kar ki manta a kulun adu'armu kennan, burinmu kennan, yau ba iya mu ba na tabata du wani masoyinmu yana cikin farin cikin wannan ranar, kuma Aunty yayanmu ne fa, kaf duniya babu wanda ya sanki ya iya zama da ke sama da shi, ba za'a yi wanda zai iya kular mana da ke kamarsa ba, aunty idan soyayyar ce ke kin san cewa........" "Rukaya, a sanina shekara uku cif na baki a duniya, idan kika kuskura kika ci gaba da kawo min zancen rainin nan tsaf zan fafala maki mari na bata ran du wani mai ji da ke, kin ga tashi ki tafi kawai!" Khausar ta fada tana jan hijabinta ta share hawayenta A'isha ta saki murmushi tana sakin labulen dakin na khausar ta yi gaba abinta, ita kam bama zata tunkari yayar tasu yau ba, shagali kuwa tana zuwa gida alwallah zata daura ta hau darduma duma wanda baya son gannin lamarin to Allah ya saka katangar karfe da su, ita kuma yayarsu tana rigimar TAUFEEK? TAUFEEK fa? Zasu gani lokaci dai! Da wannan du aka watse aka bar Khausar da Mama a gidan, Mama kuwa ta yi banza da ita dan ko abinci da aka bata ta ki ci kyaleta ta yi tace in dai yinwa ce zata fitar da ita da kanta! Kusan karfe goma sha daya Maman ta daga labule fuska a hade ta ce " ki zo in ji babanku!" Khausar ta sauke numfashi tana jin yadda kanta ke sarra mata, uwa uba yinwar dake kwakularta ga kuma tashin hankali A haka ta fito ta karasa dakin mahaifinsu ta yi salama ta rakube tana jira a bata izinin shiga , a ranta ta gama sani cewar mahaifinta in dai ya ga yau abincima bata ci ba to fa zai tsinke wannan lamari mai kama da almara wai ita da auren Besty Gyaran murya Aba ya yi yana cire asuwakin dake bakinsa a tausashe yannayin fuskarsa bayane da kyakyawar fara'ar da sam ta kasa barin fuskarsa ya bata damar shiga falon nasa Abinka da mai saida turare, dakin na Aba yau kamar turaren ya bude ya bade dakin nasa da shi, kanshi ta ko'ina haka kuma a tsaftace tsaf tsaf kamar yadda Mama ta saba sam ba zaka shiga dakin nan ka same shi da dati ba A kasa ta zauna nesa da su kadan tana jan hijabinta ta rufe fuskarta sosai da shi bayan ta ga shadar da abanta ya maka yau, watau dinki ne sabo aba ya cancara na wannan rana shada ce fara kal a jikinsa , sai kawai ta ji wani irin kuka ya kubce mata wanda ta kasa rikewa a gaban wanda ta saba yiwa shagwaba wato mahaifi Aba ya kalli mama yana dan zarro ido, ita kuma ta sake shaka , ji take yi inama in ta tashi ta dane y'ar nan ta daka babu abinda za'a yi? Sai dai ta jima da Sannin waye mahaifin ƴaƴanta a kan yaransa, bale Khausar da ta zamto wace ya fi tausayi ya fi ji a zuciyarsa Da yannayin nunin tashin hankali Aba ya ce" subahanallah, Khausar kuka kuma?" Ai kam ba ta ji ya tanka ba? A hankali ta ja jiki tana mundulawa ta karasa daf da shi ta bude kumatun nan da suka haye dan ɗorawa kai fitina tana kallonsa ta ce" Aba ba dole na yi kuka ba, dole na yi kuka Abana, shikenan wai sai na ji wai an ce wai da TAUFEEK ne aka yi, yo Aba TAUFEEK fa , TAUFEEK fa Abana abokina ne, mu sha yawon mu mu sayi awara ne, Aba har zance nice nan mai raka TAUFEEK, kuma sai ace wai shine mijina?" "To Khausar din Aba me ya fi amininka ya zama mijinka dadi a duniyar nan ta Allah?" Aban ya fada a tausashe yana fuskantarta sosai, Mama kuwa ta dantse lebe , ji take yi inama inama ya bata dama ta dan gagaurawa Khausar mari jama'a? Wannan rashin Sannin ciwon kai har ina? Khausar ta ja hanci ta ce" Ina , Aba ba dadi ko daya, ba dadi, to Aba an raina junna ai, TAUFEEK ya jima da rainani nima haka, auren nan kuwa ai sai baba da yaro ko?, Ana so namijin ya zama baba macen kuwa yarinya ba wai Ni da TAUFEEK ba Abana, Aba to yaya zan yi a wajen aiki? Shine babanmu fa, kuma shi wai dayan mema na masa ya fasa aurena?" Abanta ya sauke numfashi, cike da hikima ya ce" Ni kam yar gidan aba wani lokacin sai in ga kamar Khausar dina bata fi shekara biyar ba, tsakani da Allah mutumen da a tsaye ya fi ki tsayi , a shekaru ya baki na kirki ne kike yiwa wannan zaurancen? Kuma kike cewa aiki wani aikin kuma ke da aka daura maki aure? " A zabure Khausar ta dubi Abanta, bakinta har yana rawa ta ce" Abana aikin? Abana aikin da ya zamto burina kuma cikon farin cikinmu baki daya? Abana dan girman Allah kar a taba lamarin aikina domin Ni aikina ina yinsa ne ba dan badangarci ba, da farko na zabi fanin lafiya ne dan na taimaki bayin Allan, sai kuma ina fa bukatar aiki dan na tallafawa iyayena, Abana banda aikina banda aikina" "To wai Khausar kafin ki fara aikin Bama ci ne ko Bama sha ne ko Bama daura sutura ne?, Ki fa kiyayeni da abu kamar wace bata godewa Allah ba, yaya zakina abu kamar na jahila? Auren ai ya fi aikin daraja in kuma mijin ya ki ba zaki yi ba, ke baki ga farin cikin fuskar mahaifinki na raguwa ba ? Dan kin sani sarai komai kankantar shirmenki daga masa hankali yake, inama ya bani dama in nuna maki yadda ake godewa Ubangiji? Shashancin banza malan, ke yau mu kam ranar farin ciki ce a wajen mu in bata maki ba je ki rufe dakin ki dora daga inda kika tsaya, ana wani taroki dubeki kina jibgewa dan kin ga abanki ko? Shi TAUFEEK din bai ce baya yi ba sai ke ? Ki c............" Aba da ya zubawa bakin Mama ido yana kifta idon yana kallonta ya yi kyaftun da ya sakata dubansa a wayance haka kuma ta ja bakinta ta yi shiru ta mike tana tatara abinda batama san me zata yi da su ba ta yi waje, sosai take sama dalilin Khausar idan har ta samu dama kuma tasss zata mamaketa walahi! Aba ya jinjina kai bayan ya ga ficewar Maman, sai kuma ya saki murmushi gannin Khausar ta yi tsamo tsamo ta sake rakubewa kusa da shi , watau farar kura ga tsoro ga ban tsoro ko? Shine aka raina ake yiwa daru A tausashensa ya ce" 💔💔💔💔❤‍🩹❤‍🩹💔💔💔💔 *DA CIWO A ZUCIYATA* 💔💔💔💔❤‍🩹❤‍🩹💔💔💔💔 _MALLAKIN_ *SAJIDA NIJAR* *FREE BOOK NE* 4️⃣2️⃣ *GARABASA, GARABASA, PROMOTION, PROMOTION DIN LITATAFAN MARUBUCIYAR A KAN FARASHI MAI SAUKI 1K, YAN NIJAR KUWA 1000 FRANCS CEFA* 1: Duk karyar kada 2: Yar mahaukaciya 3: Neman na kaina 4: Bani da zabi 5: Bak'a ce 6: Kutkale 7: Makauniya ce 8: Mage 9: Duk nisan jifa 10: Idan ka raina inda kake 11: Dutse 12: Alkalamin kadarata 13: Bani da zabi 14: Dakika Biyar 15:Wata kokowar 16: Aure yakin mata 17: Ni zan ladabi 18: Daga tafia daukar soja *Dukansu a kan farashi mai sauki, zaka saka dubu guda ne domin promotion ne nake yi, ka tuntubeni kan layina kamar haka +227 93 81 16 18, Sajida Nijar* Now *Da CIWO A ZUCIYATA* *Tallah, tallah, tallah* *SECRET DE LA FEMME DU MANGA* _Gidan Kamshi, Sirrin Manyan Mata, nesa tazo kusa,Amarya ,Uwar gida,Ango da mai gida Har ma da yan mata da samari shin kuna sane da cewa HAJIYA FUSAM ta shirya tsaf domin gwangwaje ku da turarakunta masu dankaran kamshi? Tare Kayan gyaram jiki na musamman ,wanda daga nesa kamshin ki kadai ya wadatar ya isar da sakon zuwanki waje,gidan ki kuwa sai ya zam abun kwatance wajen kamshi, kar na cika ku da surutu bara in fara zayyano su_ Farar Humura Bakar Humura Humura special, humura de bain Humura epicé Lait de nuit Parfums désodorisant Parfums rideau et dras Lait de nuit Alkam Kulakcam *Waɗannan kadan ne daga bangaren turaran ruwa* Gagab, sandal flex, Durot, durus, sandal fleur, tafarce, farce, sandal bangui, sandal, hypotonic sandal, al'ut, coktail creation VIP, Gajiji, Mankaji, turaran wutar labule da cafet, Aba malan, boulettes *Munada bangaren gyaran jiki kamar haka:* mai mai saka santsin jiki, mai mai kanshi, Kayan gyaran jiki mai saka fata ta yi santsi da laushi, kayan gyaran jiki mai saka fata ta yi fari, Sabulu mai saka fata ta yi haske, sabulu mai saka fata ta yi santsi, sabulu mai goge yanayin fata, mai wanda baya saka fari mai gyara fata Sayen na gari mai da kudi gida,sai an gwada akan san na kwarai💃💃 Hajiya Fusam na zaune a kasar Niger domin yin magana da ita kai tsaye tuntuɓi wannan number 97 82 44 94 *SECRET DE LA FEMME DU MANGA* Gidan Kamshi, Sirrin Manyan Mata💃💃💃💃💃 A tausashensa ya fuskanci Khausar, a nutse ya ce" Kin ga, yar gidan Abanta, yarinyana mai albarka, yar arziki gajera yayar A'isha share hawayen mu yi magana kin ji? Share hawayenki mu yi magana" Khausar ta ringa sauke ajiyar zuciya tana kallon mahaifinta, a hankali ta ringa share hawayenta har ta share tasss tana kallonsa tana kuma sauraronsa Aba ya ce" A sanina Khausar dina tana da ilimin addini daidai gwargwado ko?" Khausar ta gyada kai tana kallon mahaifinta Aba ya ce" To menene abin rikicewar nan har haka?, Menene Khausar? Fada min menene na tashin hankalin har haka?" Ido kawai Khausar ke tsurawa waje guda, a cikin zuciyarta tarin amsoshin tambayar Aba, sai dai karfin da sukai mata a harshenta ba zata taba iya kwatantawa Aba haka din shine dalilinta, A sanyaye ta sada kanta ta ce" Abana, gani na yi tsakaninmu bamu taba magana makamanciyar haka ba, kuma fa Abana TAUFEEK ne fa, shi dinma Hajia tace bai san da zancen aure ba na dole aka masa, kuma Aba me duniya zata kalleni? Dama a anguwa ana min wannan zaton ana zagina da haka, kuma ban san shi ne na masa ya fasa aurena ba sai kawai ace da TAUFEEK?" Aba ya gyada kansa ya ce" to Ni a bayanin nan ban ga wanda ya zama rikaken hujar da zan yi duba da ita har in fuskanci kin yiwuwar auren nan ba yar gidan Aba, inace na hore ku da jin tsoron Allah kadai da kuma kiyaye hakokin musulunci, yaushe kika fara damuwa da zagin yan anguwa? Ai da kin jima a kasan kasa Khausar dan kuwa ai an jima ana zagin namu ko?, Ko dan karatun nan naki ai babu abinda bamu gani ba, Ni na fi so in akoy wani dalilinki ki sanar min sai mu duba ko yar gidan Aba? Kuma shi aure ai zuwa ake yi da zuciya daya a zauna , idan har zaman bai yiwu bane ake yin hakuri ko? Sannan maganar aikinki Elhaji ne da kansa ya ce min a jibin nan zaki koma bakin aikin ki, a gobe za'a kawo lefenki da kuma direbanki dan yace a yi hakuri da maganar shiga adaidaitar , tarewa kuma da an ce a yi da gagawa sai yace a bari har su Elhaji karamin su dawo daga haji sai ki tare, kin ga ai muna tare ko yar gidan Aba?" Khausar ta ringa kallon mahaifinta, tana gannin wani annuri a tare da shi wanda du yadda yake son boyewa ya ki boyuwa, haka kuma bayanansa sun mata wani irin girma da neman shiga kwakwaluwarta, Bama irin maganar aure zaunawa ake yi idan ta yiwu ake yinsa, hakan na nufin idan ta dawo tace masa auren nan fa ba zata yiwu ba zai raba? Kai in kuwa haka ne tana iya yin shiru har su hadu da TAUFEEK su yi shawara, ta tabata shima zai ce ne eh wannan aure son iyayensu ne ba nasu ba, Aba ya sake fuskantarta ya ce" Haka kuma, a kulun ina horarki ko me ya tunkaroki komin rikicewarsa da rikita zuciyarsa ki fadawa Allah, ki kai kukanki wajen ubangiji, ki bashi zabi kin ji yar gidan Aba, Ni kam sai in ce alkhairin ne fa, ki duba ki ga kulun adu'armu kennan fa, nan har cewa kika yi in kai ki masalaci in ba kowane nema ke dai a maki auren kema ko? Kuma yanzu Allah ya kawo sai ki ringa rigima? So kike yi hankalina ya tashi ne ?" A hankali Khausar ta girgiza kanta tana jin wani irin tausayin mahaifin nata na ratsa mata zuciya A sanyaye ta ce" Abana ka yi hakuri ka ji? In sha Allah zanma gani ne tunda kace auren ai in zai yiwu ake yi ko Aba?" Mahaifinta ya amsata, yana sake gannin tamkar wata yar jaririyarsa ne Khausar din, sam baya gannin girmanta, idan ta yi wani abin kuwa gaba daya yake gannin rashin wayonta ƙarara, cikin hikima ya idasa kashe borin rigimar, bale da ta ji cewar zata je aikinta a jibi jibinnan sai ta ringa jin kamarma auren an riga an rabashi ne, Da wannan ta fito daga dakin mahaifinta, sai tunane tunane take yi, to ita jama'a yanzun idan ta ga TAUFEEK ta ce masa me yace mata me? Tashin hankali wanda ba'a saka masa rana Ido hudu suka yi da Mama, Maman ta sakar mata harara da sauri ta sada kanta ta shige dakinta tana jan hanci ta cire zumbulelen hijab din da ta wuni da shi dan dole, ita daya sai tura baki take yi ta nemi waje ta zauna saman katifarta da yar karamar rigar dake jikinta ta barci ta shiga murza manyan cinyoyinta tana sauke ajiyar zuciya tana kallon wayarta zuciyarta cike da tunani kala kala, ita daya sai ta ja tsaki, ta yi kyaftu ta yi wannan ta yi wannan , tunani ya yi mata yawa Mama kuwa dake tsakar gida bata koma daki wajen Aba ba, tana zaune ne da autanta suka gama waya da Rukaya wace ke shaida mata cewar gobe da safe mai kitso da kunshi zasu zo a yiwa auntyn tasu dan Allah maman ta tirsasata ta zauna a yi mata tunda an ce jibi zata koma aiki sunna so ta koma a matsayin amaryar , Allah ya taimake su yanzun auntyn tasu ita da kanta tana dan gyara fuskarta in zata fita, dama fannin turare ba'a maganarsa da tsafta domin Khausar akoy tsafta Washe gari Kusan karfe bakwai na safe Hajia Fatahiya ta yi salama a bangaren TAUFEEK sannan ta dakata kamar yadda Mama, fa Hajia nawarah da shi kan Mai kwanonin ke tsaye sunna jira a basu damar shiga, sakamakon zuwan Hajia ta wanke su tassss ta dawo bangaren domin a nan ta kwana ita da Yumnah a falon tana yi tana leka shi har asubahi ta yi itace ta koma ta aniya taimaka masa har ya mike bayan yana iyawa tace zata raka shi har bayin sai da ya kiya ne ta samu ta fice ta je bangaren Aban ta masa tasss sannan ta bi daki daki ta masu tasss ta koma harda hawayenta wai magidanci ba lafiya bata ga kafar kowa ba Yumnah ta ja numfashi, ranta cike da jin haushin Hajiar nan, ta sakata ta soya wainar kwai ta zauna tana bashi a cokali kamar ita ta haifeshi, shi kuwa sai wani lumshe ido yake yi jikinsa har yanzu da zafi ama ya ki zuwa asibitin kuma ya ki korar wannan masifafiyar tsohuwar ta saka mata falo banda kaurin jiji babu abinda yake yi wai ita bata iya zama sai da turaran wuta, du tarin turaran wutarsu ta je ta kwaso jijinta ta ringa maka masu a falo kamar gidanta Mikewa ta yi ta je ta bude dan yadda aka dannan karaurawa aka kuma yi salama ta tabata masu son shigowar manya ne, dan bata taɓa gannin kaffafuwan yaren gidan a bangarensu ba Budewa ta yi, sai kuma da sauri ta bada hanya tana amsa salamar Su Hajia ne suka fara shiga, sannan Mama sai kuma Baban shima ya shigo da suturarsa mai kamala hannunsa da carbi da hularsa a kansa domin shi ma'abocin fita da hula ne ko a cikin gidansa Mama ce ta fara karasawa daf da Hajia ta duka har kasa tana gaisheta, kishiyoyinta suka mara nata baya , sai uwa Uba Aba ya karaso shima da kuzarinsa ya duka har kasa yana cire hular kansa ya ce" Barka da safia HAJIA, fatan an tashi lafia?" Hajia ta yamutsa fuska tana kallon TAUFEEK dake kokarin tashi daga kujerar da ta saka shi a gaba ya duka shima kansa a kasa yana gaisar da iyayen nasa , ama babu wanda ya amsa tunda amsar ta Hajia suke jira kafin su iya amsawa, sai ya zamto Yumnah itama a dole ta duka din gannin harda baban a duke gaban wannan mai fuska a haden Hajia ta sake hade fuska ta ce" Kwana ku kuka ganshi Ni ban ganshi ba, dan kuwa kwana na yi ina fama da jikana, ba lafia numfashinsa da kyar yake fita , hannuna a saman daidai zuciyar magidanci haka kirjinsa ke bugawa , Yaren nan sam bakwa jin tsoron Allah, ban san me yaron nan ya tsare maku ba fa kuka tsane shi, a zo a kama min a kai min shi asibiti kuka kiya kuka je kuka kwonta, wai harda ke da kai, in su Wadinnan basu san zafinsa ba ai bai dace ace harda ku ba, daga yau na san zaman da zan yi da kowa a gidan nan, kuma babu wanda zai yi ciwo mu damu Ni da Magidanci, gaisuwa ku rike abinku bana so, wulakancin banza da wofi!" Taufeek ya zuba mata ido kasa kasa ya sakar mata harare, ita kuma ta tsuke baki ta ce" Ka harari wannan, kai yanzu du abinda suka maka dan rashin zuciya sai ka ji ciwo in na masu fada ko?" Aba ya yi murmushi kansa a kasa ya ce" a yi hakuri Hajia mun yi laifi, a yi hakuri ba zamu sake ba in sha Allah, ai jiyan kin ga baki ne basu tafi ba sai dare, masha ALLAH daurin auren kamar da wasa ya tara jama'a kuma aka zauna sosai sai da muka ci abinci aka yi zumunci sannan aka watse" Hajia ta yi dan shiru sai kuma ta sauke ajiyar zuciya ta ce" Ni walahi du sai da abin ya min lami, ita KHausarar fa har kamar zata summa wai bata so, bata son magidanci fa, kuma na taho nan dan in ganshi na tardashi ba lafiya abin sai ya rikitani, auren nan du sai ya shige min, to yaya ka barota ita KHausarar ?" TAUFEEK da kansa ke kasa , a kasan dai yake, sai dai a bayanin kakarsa ya dan so shiga hali na rudu kadan, Magidanci dai du duniyar nan daga bakin Hajia shi ake nufi, to meye hadin maganar bata sonsa Khausar kuma? Aba cikin murmushin ya ce" Ai haka dai aka bata hakuri, sosai ta nuna bata so din, ama an rarasheta tunda an riga an daura ai hakuri za'a yi, kuma tsakaninta da Elhaji karamin ai sun fi kusa , zasu daidaita kansu ne bi izinillah " Yanzun kam dago kai ya yi ya zubawa mahaifinsa ido, hakama du wani wanda ke wajen ama banda Mama wace ke murmushi itama ta diramar mijin nata da sarakuwarta Hajia ta yi murmushi gannin yannayin TAUFEEK, ta mike tana fadin" Ku karaso mu zauna a yi maganar abinda ya faru jiya, ke yaminah je sako hijab mana in Ni kin rainani kina yawo da rigar nan da hula a gabana Wadinnan din ai sirikanki ne harda uban mijinki ai da kunya ko?" Yumnah ta zubawa Hajia ido, idan har zata iya zuwa dakinta a irin wannan lokacin ai tana iya zuwa ko'ina ma Bata tunanin ko zata iya zuwa wani daki sako hijab maganar da baba ke yi ke neman sakata juwa, dan haka ba tare da ta je din ba ta karasa kusa da TAUFEEK ta zauna a saman kafet din kamar yadda ya yi sannan ta zubawa Baba ido wanda ke saman kujera , hakama su Hajia Dukansu a saman kujerar suke A nutse Baba ya ce" Assalamu alaikum wa rahamatulah, kamar yadda Hajia tace, haka ne, ina son sanar maku ku dukanku abinda ya faru jiya, alhamdulilah daurin auren da muka je da Magidanci aka daura shi , wannan din hukunci ne na Ubangiji, haka Allah ya so, da wannan nake dubanki Yumnah kan maganar, na san me mata ke daukan abokiyar zama, haka kuma ana iya fasarar cewa baki jima a gidanki ba hakan ta faru, ki Kadara cewa Allah ne ya hukunta haka a rayuwarki, dan kin ga Hajia gatanan da mahaifiyar mijinki rana daya na aure su, kowani bawa da irin kadararsa mijinki kansa bai san cewa san daura aurensa da KHAUSAR ba, ita dinma cikin firgicin abin take harda kukan bata so, to gaba daya dai hakuri za'a ba kowa da kuma fatan Allah ya sa KHAUSAR alkhairi ce a garemu baki daya, ban nemawa mijinki auren Khausar dan na ga gazawarki ta kowani fani ba, ban kuma yi haka dan wata mummunar manufa ba, Allah ne ya Kadara ita din matar mijinki ce , ina fatan zaku mana biyayya gaba dayanku ku zauna lafiya" Hajia ta saki wani murmushin gannin irin zazaro idannuwan su Hajia nawarah da ita din kanta Yumnar, Mama kuwa kanta a kasa dama bata dago ba, dan bata da ta cewa a taron da bayanin TAUFEEK kallon fuskar mahaifinsa yake yi tamkar ya ga bako a duniyarsa, Hajia ta gyara zamanta ta ce" To hakurinma da kake badawa Ni ban ga laifin da aka yi ba, aure fa aka ce, in ba'a yi ita aka aurota? Kawai dai batun kishiya ne ba dadi ama in ta yi duba da khausara ai dama kishiyarta ce ba yau ba sai ta ba kanta lafiya a zauna lafiya, magidanci kuwa Ni dama ina hango shi a mace hudu ne, dan in ka yi duba da auren nan sunna ce ta ma'aiki, jikana kuwa baya tsoron uban kowa bale ya ki jera hudu ana masa cenji cenjin tukunya yana rayuwa tamkar da Sarki wannan shine more rayuwa, itama Khausarar da take kukan bata son shi zan koma ne, na sameta , babu mai hannani wanka mata mari a kan magidanci!" TAUFEEK a hankali ya maida idannuwansa ya lumshe , daga zaunen da yake ya gama gane Yaren mahaifinsa da kuma kakarsa, ana nufin cewa auren da aka daurawa Khausar aminiyarsa a jiya da shi ne aka daura shi? Idannuwan nasa ya so budewa a hankali, sai dai da sauri ya bude su sakamakon faduwar Yumnah saman kansa rana jan numfashinta da dukkan karfinta hannunta a damke da rigarsa tana kallonsa a hankali idannuwanta suke rufewa har ta rufe su ruf still tana jan numfashin nan da kyar tamkar wace zata bar duniya A rikice du suka mike, Bama kamar su Hajia Nawarah ba sunna Salalami , dama tunda Baba mai kwanoni ya fara bayanin nan suka kasance a kololuwar mamaki sunna binsa da kallo sai zubewar Yumnah ta saka su mikewa sunna neman daukaka abin fiye da misali Hajia ta rafka salatin itama tana gannin yadda su Hajia suka talafo Yumnah ama ta ki sakin rigar TAUFEEK, haka kuma numfashinta da gaske sama sama yake yi tamkar wace zata summe Da tarin al'ajabi Hajia ta ce" Wai summa ta yi? La ila ha ilalahu Muhammadu rasululahi sallalahu alaihi Wasallam, summa ta yi daga mata abokiyar zama ko me ?" A tausashe TAUFEEK ya kalli Hajiar kasa kasa ya ce" Ki daina ihun nan mana ki yi a hankali bakya gannin halin da take ciki?" Hajia ta yi tsuru tana kallon yada yake magana da wani yannayi na lisilama, sak kamar munafuki, in ba mantawa ta yi ba dazunma da tana bashi abinci ai magana ne ya kasa kuma ya kasa ci da kansa ko? Yaushe ya samu lafiyar talafar wannan tabaryar har yake son mata iya shege? Baba ne ya budi baki shima hankalin nasa a tashe ya ce" Alhamdulilah, mun fa dawo, sai fatan Allah ya bamu ikon yin typing lafiya, ya kuma bamu ikon farantawa junna *DUBUN GAISUWA DA FATAN ALKHAIRI ZUWA GAREKU YAN UWA DA AMINAN ARZIKI, SPCLY SAJIDA PALACE, MEMA ZAN CE? TA INA ZAN FARA? A INA ZAN SAUKE? ADDU'A ITACE TSAKANINA DA KU DA FATAN ALKHAIRI, KUN YI RAWAR GANI NA MAMAKI, KAMAR YADDA KUKA SABA KUN YI MIN ALKHAIRI FIYE DA TUNANINA, ALLAH YA SAKA DA MAFIFICIN ALKHAIRI, ALHAMDULILAH Y'ARKU NA GODIYA, ALLAH YA BIYA, WA'INDA SUKE TAMBAYANA DALILIN SHIRUNA DA YAWA KU YI HAKURI HAIHUWA NA YI SHI YASA, WA'INDA BAN AMSAWA BA KU GAFARCENI , WALAHI MSG DIN DA YAWA SOSAI FA, INA FATAN ALKHAIRIN ALLAH YA KAI MUKU A DUK INDA KUKE, KUN SHIRYA JIN ME ZAI FARU A RAYUWAR KHAUSARA YAR GIDAN ABA DA AMININTA DA KUMA ABOKIYAR ZAMANTA? ME ZAI FARU TSAKANIN MAMA DA ABOKANAN ZAMANTA? MU KAFTA PEOPLE😌😌😌* 💔💔💔💔❤‍🩹❤‍🩹💔💔💔💔 *DA CIWO A ZUCIYATA* 💔💔💔💔❤‍🩹❤‍🩹💔💔💔💔 _MALLAKIN_ *SAJIDA NIJAR* *FREE BOOK NE* 4️⃣3️⃣ *GARABASA, GARABASA, PROMOTION, PROMOTION DIN LITATAFAN MARUBUCIYAR A KAN FARASHI MAI SAUKI 1K, YAN NIJAR KUWA 1000 FRANCS CEFA* 1: Duk karyar kada 2: Yar mahaukaciya 3: Neman na kaina 4: Bani da zabi 5: Bak'a ce 6: Kutkale 7: Makauniya ce 8: Mage 9: Duk nisan jifa 10: Idan ka raina inda kake 11: Dutse 12: Alkalamin kadarata 13: Bani da zabi 14: Dakika Biyar 15:Wata kokowar 16: Aure yakin mata 17: Ni zan ladabi 18: Daga tafia daukar soja *Dukansu a kan farashi mai sauki, zaka saka dubu guda ne domin promotion ne nake yi, ka tuntubeni kan layina kamar haka +227 93 81 16 18, Sajida Nijar* Now *Da CIWO A ZUCIYATA* *Tallah, tallah, tallah* *SECRET DE LA FEMME DU MANGA* _Gidan Kamshi, Sirrin Manyan Mata, nesa tazo kusa,Amarya ,Uwar gida,Ango da mai gida Har ma da yan mata da samari shin kuna sane da cewa HAJIYA FUSAM ta shirya tsaf domin gwangwaje ku da turarakunta masu dankaran kamshi? Tare Kayan gyaram jiki na musamman ,wanda daga nesa kamshin ki kadai ya wadatar ya isar da sakon zuwanki waje,gidan ki kuwa sai ya zam abun kwatance wajen kamshi, kar na cika ku da surutu bara in fara zayyano su_ Farar Humura Bakar Humura Humura special, humura de bain Humura epicé Lait de nuit Parfums désodorisant Parfums rideau et dras Lait de nuit Alkam Kulakcam *Waɗannan kadan ne daga bangaren turaran ruwa* Gagab, sandal flex, Durot, durus, sandal fleur, tafarce, farce, sandal bangui, sandal, hypotonic sandal, al'ut, coktail creation VIP, Gajiji, Mankaji, turaran wutar labule da cafet, Aba malan, boulettes *Munada bangaren gyaran jiki kamar haka:* mai mai saka santsin jiki, mai mai kanshi, Kayan gyaran jiki mai saka fata ta yi santsi da laushi, kayan gyaran jiki mai saka fata ta yi fari, Sabulu mai saka fata ta yi haske, sabulu mai saka fata ta yi santsi, sabulu mai goge yanayin fata, mai wanda baya saka fari mai gyara fata Sayen na gari mai da kudi gida,sai an gwada akan san na kwarai💃💃 Hajiya Fusam na zaune a kasar Niger domin yin magana da ita kai tsaye tuntuɓi wannan number 97 82 44 94 *SECRET DE LA FEMME DU MANGA* Gidan Kamshi, Sirrin Manyan Mata💃💃💃💃💃 Baba ne ya budi baki shima hankalin nasa a tashe ya ce" Subahanallah, yaya kun ririketa kun gaza dagata, dagata TAUFEEK mu je asibiti dagata mu je" Mama dake tsaye tana jiran gannin su Hajia in kamata zasu yi su kamatan ama sai wani daukaka abin suke ne, Hajia baba kuwa dama hannayenta biyu a kirjinta banda harara babu abinda take makawa magidanci dan bata taɓa tunanin zai samu karfin tare wannan matar ba shi da ba lafiyar kirki ne da shi ba? A nutse mama ta dan matso ta ce" Hajia dan gyara in gani" Hajiar ta dago ta dubi Mama, ta ga Maman sosai fuskarta a hade, abinda bata taɓa gwadawa ba, kai abinda ya shafi magidancin nema Maman tana matukar nuna kara da kauda kai, da dan mamaki ta matsa din ta bata waje Da kula sosai Maman ta ce" Sai an kaita asibiti ne? Numfashin nata nake gani sama sama Elhaji?" Shi da kansa ya yi mamakin wannan lamari na mama duda halin da yake ciki na rabuwar tunani da kuma matarsa mai dauke da dan tayin cikinsa dake kwonce saman jikinsa idannuwanta a rufe ruf tana kokowa da numfashinta, da kula ya ce" Yumnah, Yumnah hey......" Mama ta duka daf da su sosai , da kula ita dinma ta dafa bayan Yumnar a hankali tana dan shafa kanta ta ce" Daughter, Please calm down, kin san halin da kike ciki kar ki janyowa kanki wani ciwo a kan abinda ya riga ya faru, Please calm down...." Hajia Baba ta sake yin KISKIRIM tana bin kowa da kallo Baba dake tsaye ya bi Hajia Fatahiya da ido wace ta fita tana dana waya cike da basar da uban kowa, wayar Tata kuwa ba kowa take nema ba sai uwar Yumnah, domin tsabar bin salsala irin na kuturta bin dan aboki har numbar junna ne da su sunna zumunci irin nasu Baba ya ce" Ka dauketa mu je asibiti ba wata kama ce da ita ba?" Sai yanzu TAUFEEK ya sauke ajiyar zuciya , shi kokarinsa na gannin ta daina jan numfashinta ne, ama firr abu ya gagara , dan haka ya mike tsaye tsaf da ita a jikinsa tamkar ya dauki yar jaririya ya juya ya nufi hanyar fita da ita dan bin umarnin iyayensa cewar a sadata da asibiti Hajia ta rafka salati harda talabe haba, tana biye da su ta dan riko hannun baba ta ce" Ka san wa bilahilazi yaron cen dazu sai da na masa dan jagora na fitar da shi daga dakinsa na sauko shi kasa na bashi abinci, dan sak yace da Ni baya gani jinninsa ya hau, ka ga wannan abar ta suma ya dauketa, to ko dai Mayu suka rike shi kuma yanzu suka sake shi da na yi da gaske?" Baba mai kwanoni ya yi murmushi ya ce" Hajia ai saukin dai ya samu ne kawai, Allah dai ya tsare gaba" Har kusan babar motarsa suka karasa Mama ta bude bayan motar ta shiga ba tare da ta bada damar wata zata rakata ba ta masa alamar ya sako Yumnar Hajia ta zagaya gidan gaba ta bude ta shige tana fadin" Mika mata ita mu je, bayanin dan tayin nan ya fi komai tsaya min a rai mu je , sai mun dawo " Baba mai kwanoni ya yi murmushi bayan motar ta fice a gidan, watau sosai ya yi mamakin mahaifiyar TAUFEEK yau gannin idonsa itace ta yi gaba da lamarin yaronta, ya kuma ji dadi mai girman gaske, sai kuma TAUFEEK din dake hade girar sama da ta kasa na rashin kunya Sunna isawa asibitinsa kamar yadda dokar wajen take idan har aka kawo daya daga cikin dangin wani ma'aikacinsa, Wada suke da kusanci sosai kama daga mahaifiya, mahaifi, mata, ya'ya to ba za'a duba marar lafiyar da mutumen ba dan gudun rikicewa da sauransu , dokar kuma na kan kowa ne ba iya ma'aikatan ba, har shi mai wajen, dan haka sunna isawa aka dorata a kujerar tura marar lafiya aka shige da ita bangaren emrgency, shi kuwa ya zauna a office din doctern dake aiki a ranar a hankali ya jinginar da bayansa bayan doctern ya fitar masa da ruwan roba ya ajiye masa sannan ya fita da sauri ya tarda abokanan aikinsa dan bata taimakon gaggawa Cikin ikon Allah a lokaci kankanin aka samu aka daidaita bugawar zuciyarta sannan aka tsayar da zubar da jinin da ta fara , sai dai kukan da take yi sun gaza hannata shi, sun yi iya yinsu dan gannin ta daina kukan ama ta kiya, uwa uba tunda suka daidaita harkar bugawar zuciyarta ya zamto ko me aka zo za'a saka mata sai ta karanta a zaune cir a saman gadon take hakan ya sa ta ki a saka mata alurar barci, abinka da wace take da damar dakatar da su din ne, domin da wani ne gaskiya Bama zai tarki haka ba Docter Muktar ya dubi Nurse Halima da kula ya ce" Ina ga ki tabo docter, dan kar ya mana fadan cewa a kan me zamu saurari ra'ayinta kin san baya son wasa da irin haka" Nurse Halima ta fitar da numfashi tana cire safar hannunta ta ce" Ok docter" Fitowa ta yi da dan gaggawa dan karasawa office din docter Ahmad din dan ta isar da sakonsa, sai dai tana fitowar ta samu wajen dakatawar ya cika sosai, dan kuwa matan Elhaji mai kwanonin sun karaso su dukansu, haka kuma mahaifiyar Yumnar da yayarta wace ta zo gannin jikin mahaifinsu da ya yi yar jinya su dinma sun karaso din, sai dai yannayin mahaifiyar Yumnar sam ba alamun sassauci a fuskarta kamar yadda yannayinta yake Tunkarar Nurse Halima ta yi , fuskarta a hade hakama yannayinta ta ce" Nurse yaya jikin yarinyata? Ina fatan tana iya mikewa mu je gida?" Yayar Yumnah dake tsaye kusa da Hajia ta yi gagawar kallon mahaifiyar Tata, 'ya ALLAH' shine abinda ta ayana a cen kasan zuciyarta, shin yaya zata yi da wannan fitina ne? Ama a gaskiya wannan mata da ta kirayi mamansu ta ziga rikicin nan bata yi masu adalci ba, yanzu gashi tunda mahaifiyarsu ta zo ko gaisar da iyayen TAUFEEK din bata yi ba sai fizge fizge take yi har ta saka Hajia gaishe da ita cike da mamakinta, sai kuma ga wata Maganar? Nurse Halima da kula sosai ta ce" Sorry Hajia, matar Sir ce a ciki, jikinta da sauki sosai sai dai ba maganar tafiya da ita yanzu, ki dan yi hakuri zan je wajen sir din ne" Da sauri mahaifiyar Yumnah ta dan tareta ta ce" ki dan dakata, ina son shiga ganninta, du wani wanda zai ce wani abu a kanta bayana yake dan nice mahaifiyarta, ina bukatar a bani y'ata na cenza mata wata asibitin!" Da sauri yayar Yumnah ta matso ta ce" Mama, dan Allah ki yi hakuri ki zo ki zauna" Rai bace ta juyo tana daga hannunta kusa da ita ta ce" Ke Akilah walahi idan kika yarda kika kawon raini a wajen nan zan dauke fuskarki da mari, in ke baki san zafin Yumnah ba Ni na san ciwon abata idan ba zaki iya ganni ba kauce ki koma gida!" Wani tsadadan murmushi Hajia Fatahiya ta saki tana sake talabe jaririyarta, hakama Hajia Nuwairah ta dauke kanta tamkar basa wajen Hajia ta shiga rafka salati tana kallon mahaifiyar Yumnah, lokacin ne kuwa Nurse Halima ta wwucewarta dan ta kula abin na nema ya zama family isu Hajia ta ce" Ikon Allah, wai kamar wace kike yade yaden magana a wajen nan , Ni wama ya sanar maki da maganar nan ne? Mu bamu isa mu kula da ita bane sai an taso ki? Aure ne fa aka daurawa magidanci Bama shi ya je ya nemi auren ba shine zaki zo kamar kubunuwa kina magangannu kamar wace ke daf da kyatsa ashariya? Allah dai ya sa ba magidanci kike son fadawa magana ba , dan da wahala na iya kawar da kaina kowani shashasha ya wulakanta min jika, da kika ganni nan babu irin fadan da ban gani ba, ke karama ce, in zaki nemi kawo min raini a duniyar magidanci in dauke fuskarki da mari ba wani abu bane a wajena! Ke yau ga salamamiya, an yiwa yar taki kishiya kuma ubanda ya kirayeki ko waye ya kuka da kansa, ai ji ji zaki yi dan ba abin a boye bane, yaro kuwa da kudinsa da lafiyarsa akoy wanda ya isa ya tsayar da shi a daya kwalin kwal ? Ai hudu cifff zai jera maki gani ya kauda idannuwansa!" Hankali tashe Akilah ta karasa tana kokarin riko hannun Hajia ta ce" Hajia, dan Allah ki yi hakuri, duka abin nan an samu rashin fahimta ne, irin yadda aka sanar da momynmu maganar auren da rashin lafiyarta ne ya tayar mana da hankali, ama ba maganar wulakanta TAUFEEK,, itama momy ba zata yi haka ba , an riga an zama daya ai du wata fitina ana fatan Allah ya tsare ta, aure kuwa ai nufi ne na Allah dan ya yi aure ai ba shine damuwar ba in dai mutuniyar kirki ce fatanmu Allah ya hada kansu ya bada zaman lafiya............" Magana Akilah ke yi da dukkan gaskiyarta, burinta ta katse fitinar da take gannin na kokarin Kunno masu a tsakaninsu, bayan ita fitina farkonta aka sani ba'a san karshenta ba, kuma ko ba komai a duniyar hausawa ake kuma musulmai, idan har aka yi duba da irin yannayinsa bata san lafiyarsa ba ama a tsarin dukiya da yannayin nasabarsa tara mace hudun da kakarsa ke ambata ba laifi bane, dama an umarta a yi idan za'a iya kula da su a fita hakinsu ne, a nan bata ga abin rikicin nan ba, abinda ba'a yiwa kanwarta adalci ba daya ne tak, shine aka yi ba'a sanar mata ba, dole ne a ji ba dadi, ama idan rai ya bace hankali ya tashi sai a yi shiru a yi ta ambaton sunnan Allah sai ka ga komai ya zo da sauki Tana rike da hannun Hajiar wace ta zuba mata ido tana kallonta alamun jikin Hajiar kamar ya fara yin sanyi jin kalaman Akilar suka ji an fizgo Akilar, basu yi wata wata ba suka ji dauke fuskar Akilar da zazafan marin da ya saka MAMAN TAUFEEK dago kanta daga wajen da take kallo tana jan carbinta irin na jikin yatsar nan fari kal mai yar kyalkyali a jikinsa ta sauke dubanta a kan su gaba dayansu, daidai lokacin ne kuma TAUFEEK ya karaso, ya dan samu tsaikon isowar ne sakamakon rigar aikinsa da nurse Halima ta je cen sama office dinsa ta dauko masa da takalmin aiki da Safar hannu da abin auna awon zuciya A nutse yake karasowa, idannuwansa a kansu baki dayansu, tun daga kan iyayensa har na matarsa A hankali ya sauke dubansa a kan Akilah, wace ta dafe fuskarta kanta a kasa tuni hawaye ya fara wanke mata fuska, a haife ko Akilah ya girma bale Yumnah, sai dai a yadda take mutuntashi yakan ce mata auntynmu , itama sai tace da shi yayanmu dan girmama junna Kai ya dauke ba tare da ya iya cewa kowa komai ba ya ratsa su, cike da kamala da yannayi irin na baban likita ya shige ciki, hakan ya sa gaba daya suka bi shi da kallo kowa na ayana abinda yake ayanawa a ransa dangane da dan uwansa a kan TAUFEEK din Yana shiga dakin ya karasa wajen allurar da docter Muktar ya haɗa ya amsa a nutse ya karasa gaban gadon nata ya janyo kujerar dake gaban gadon ya zauna sannan ya zuba mata ido bayan ya dauki audugar da zai yi anfani da ita dan yi mata allurar tunda ba karin ruwa ta yarda aka jona mata ba Numfashi ta ringa ja tana kallonsa, kallo irin kamar ta ga wani maciyin amana, dubansa take yi kamar wace ta ga bakinta, tarin hawayen da ya cika gurbin idannuwanta kuwa na masa nuni da tashin hankalin dake saman harshenta, sai dai tarin firgicin da ya sameta, da irin yadda ya kasance mai tasiri a dukkan motsinta ya hannata iya budar baki bale har ta masa rikicin da take jin tana iya yi masa a kan maganar da ta gama yankewa kanta ko ita ko wace ake nufin an aurawa mijinta! A hankali ta budi bakinta gannin ya kama hannunta ya daura yar igiyar da zata bashi damar samun jijiyar da kyau sannan ya rike audugar a nutse ya goge bayan hannun nata, ita kuma ta budi baki ta ce" Yayanmu, dan Allah ka ce min ba zaka iya amsar auren nan ba, na san ba son ranka bane, kana da damar sakin............." "Yumnah" ya fada a hankali, cike da fitar da amon da ya fi kasarata, ya tsare idannuwanta da manyan idannuwansa, a dole ta sauke dubanta kan sajensa domin kallon ya matukar mata girma A nutse ya maida dubansa ya soketa da allurar ya kunce daurin ya zuba mata ruwan allurar sannan ya zage ya dane da audugar ya ajiye allurar a cikin dan kwanon da nurse ke rike da , shi kuwa yana rike da hannun nata a hankali yana dan murzawa yana kallon fuskarta mai zubar da hawaye har ya dauki mintinan da zasu kai sha biyar sannan ya mike yana gyarata gaba dayanta ya rufa mata abin rufa kadan sannan ya juya bayan ya daidaita mata ac ya fice a dakin yana cire safar hannunsa Yana fitowa ya ja ya tsaya gaban ahalinsa, a yadda ya shige ya barsu yanzun basa hayaniyar, sai dai kana ganninsu ka san kowa a dane yake, sai kuma ya fuskanci abinda ya hanna su hayaniyar vigil din dake tsaye su hudu ne kowane ya hade girar sama da ta kasa sun fada masu cewar du fa wanda ya masu hayaniya fitar da shi zasu yi Da kula ya ce" 💔💔💔💔❤‍🩹❤‍🩹💔💔💔💔 *DA CIWO A ZUCIYATA* 💔💔💔💔❤‍🩹❤‍🩹💔💔💔💔 _MALLAKIN_ *SAJIDA NIJAR* *FREE BOOK NE* 4️⃣4️⃣ *GARABASA, GARABASA, PROMOTION, PROMOTION DIN LITATAFAN MARUBUCIYAR A KAN FARASHI MAI SAUKI 1K, YAN NIJAR KUWA 1000 FRANCS CEFA* 1: Duk karyar kada 2: Yar mahaukaciya 3: Neman na kaina 4: Bani da zabi 5: Bak'a ce 6: Kutkale 7: Makauniya ce 8: Mage 9: Duk nisan jifa 10: Idan ka raina inda kake 11: Dutse 12: Alkalamin kadarata 13: Bani da zabi 14: Dakika Biyar 15:Wata kokowar 16: Aure yakin mata 17: Ni zan ladabi 18: Daga tafia daukar soja *Dukansu a kan farashi mai sauki, zaka saka dubu guda ne domin promotion ne nake yi, ka tuntubeni kan layina kamar haka +227 93 81 16 18, Sajida Nijar* Now *Da CIWO A ZUCIYATA* *Tallah, tallah, tallah* *SECRET DE LA FEMME DU MANGA* _Gidan Kamshi, Sirrin Manyan Mata, nesa tazo kusa,Amarya ,Uwar gida,Ango da mai gida Har ma da yan mata da samari shin kuna sane da cewa HAJIYA FUSAM ta shirya tsaf domin gwangwaje ku da turarakunta masu dankaran kamshi? Tare Kayan gyaram jiki na musamman ,wanda daga nesa kamshin ki kadai ya wadatar ya isar da sakon zuwanki waje,gidan ki kuwa sai ya zam abun kwatance wajen kamshi, kar na cika ku da surutu bara in fara zayyano su_ Farar Humura Bakar Humura Humura special, humura de bain Humura epicé Lait de nuit Parfums désodorisant Parfums rideau et dras Lait de nuit Alkam Kulakcam *Waɗannan kadan ne daga bangaren turaran ruwa* Gagab, sandal flex, Durot, durus, sandal fleur, tafarce, farce, sandal bangui, sandal, hypotonic sandal, al'ut, coktail creation VIP, Gajiji, Mankaji, turaran wutar labule da cafet, Aba malan, boulettes *Munada bangaren gyaran jiki kamar haka:* mai mai saka santsin jiki, mai mai kanshi, Kayan gyaran jiki mai saka fata ta yi santsi da laushi, kayan gyaran jiki mai saka fata ta yi fari, Sabulu mai saka fata ta yi haske, sabulu mai saka fata ta yi santsi, sabulu mai goge yanayin fata, mai wanda baya saka fari mai gyara fata Sayen na gari mai da kudi gida,sai an gwada akan san na kwarai💃💃 Hajiya Fusam na zaune a kasar Niger domin yin magana da ita kai tsaye tuntuɓi wannan number 97 82 44 94 *SECRET DE LA FEMME DU MANGA* Gidan Kamshi, Sirrin Manyan Mata💃💃💃💃💃 Da kula sosai ya ce" Alhamdulilah ta samu barci, ku mu je a maida kowa gida dan basa yarda da yan jinya" Mahaifiyar Yumnah cike da gannin rainin hankalin TAUFEEK ta ce" Basa bari ko baka bari, ko kana tunanin har yanzu bamu san wanene kai da matsayinka ba? Bama wannan ba, Taufeek bani da muradin a kula da ita a wajen da ake neman ranta, ko shekara bata rufa ba an dankara mata uwar mata, wa ya san me zai sameta idan na tafi na barta, a bani y'ata kawai a tafi da ita gida mu yi jinyarta a cen!" Ta karashe tana fitar da huci, daci take ji a ranta sosai na wannan lamarin, babu irin tarewar da basu yiwa wannan abin ba ama a karshe sai da wannan anobar ta zama mata a wajensa? Lalle da take kwabar Yumnah cewar ta daina tunanin akoy wata mu'amala da ta wuce soyaya da abotakantaka tsakaninsa da wancen guzumar yanzun itama ta fara tunanin ta yiwu wata jarabar ta bulo aka yi wannan auren rufa rufar dan kar a ji! Murmushi mahaifiyar TAUFEEK ta yi tana girgiza kanta Shi kuwa cikin nutsuwa ya saukewa vigil din dake tsaitsaye duba, kafin kace me sun yi gaba sun bar wajen Hajia baba ta girgiza kai cike da tarin takaici ta ce" Kai, fito mata da y'ar ta tafi da Itan mana sai me, wato ke ana baki kina roko kema nan uwar y'a kike ko? To bari ki ji da bakina ina waje a raye babu mai dagawa magidanci hankali, aikin banza wannan har matar huce haushi ce? In ba rashin daukan shawara Bama , ai macen farko rusasa ake dauka gidan hakuri gidan huce haushi idan ya so daga baya sai a bi dadi duniya yan idan Kanada shi ake iya zama da kai in baka da shi ba'a iya zama da kai!, Aikin banza ke kuwa kina tsaye ana neman zagar maki d'a sai dai ki yi murmushi , shin zafin nakuda aka fi ki sani ko amfanuwa yarta ta fi d'anki? Idanma zafin fitar kai ne ai na magidanci zai fi azaba, ke dai Allah ya shiryeki!" TAUFEEK ya idasa sauke dubansa a kan Hajia , ikon Allah yake kallo, Hajia da hijab kamar zai tadeta ta fadi ama banda neman rigima ba komai a cikinta, Kai ya girgiza ya juya zai bar masu wajen mahaifiyar Yumnah da take ji inama inama idan ta bude baki ta durawa uban kowa zagi babu abinda za'a yi, ama tana tsoron wannan dakewa ta TAUFEEK da kuma sharewar da mamansa ta yi, bata san me hakan ke nufi ba, ta sake dubansa ta ce" Yaya zaka tafi bayan na fada maka ina so a fito min da ita mu tafi gida?" TAUFEEK ya dakata da tafiyar da yake yi ya juyo, a hankali ya washe fuskarsa daga yannayin hadewa ya dan saki murmushi ya ce" Cewa na yi kowa ya koma gida, zan kawo ta idan na ga zata iya jurewa hakan" Daga haka ya yi tafiyarsa Mahaifiyarsa ta yi murmushi ta dauki ledar goron Hajia da ta yar tana masifa ta ce" Hajia mu je a maida mu gida" Hajia da ta gama summa a tsaye gannin badalar da Magidanci ya aikata ta ja numfashi ta ce" Eh kaini gidan dai na ga mai Kwanoni, kin ga kuma yannayin magidanci ya bani tsoro gaba dayanmu ya hade ya kora, Ni uwar mai kwanoni harda Ni? Mu je mu je" Da sauri Akilah ta fice itama a wajen ta bi bayan su Mama, har Mama ta shiga Mota ta dakata gannin ta karaso Tsayinta ta rage sosai ta ce" Mama dan Allah ku yi hakuri da abinda ya faru, in sha Allah idan mun je gida komai zai daidaita" Mama ta sakar mata murmushi cike da gannin girmanta, sosai yarinyar ta birgeta, da kula sosai ta ce" Kar ki damu auntynsu, ba wani abu kin ji? Allah ya bata lafiya, a kuma yi hakuri abin ne ya zo a haka, kin san aure da haihuwa ke da komaima na rayuwa lokaci ne, Allah ya yi haka zata kasance, kwarai ba'a kyauta mata ba, kuma Ni mace ce na san me muka dauki kishi, ama ina mai bata hakuri kuma in sha Allah Elhaji karami zai yi adalci a tsakaninsu" Daga haka suka yi mata salama direban da TAUFEEK ya sa ya kai su gida ya ja motar Sai da suka yi nisa Hajia ta ce" Uhum, wani lokacin sai ki yi halaya na munafukai sak , yo me kika masu da zaki basu hakuri? Aure fa an daura sai dai a ci da haka, Ni abinda nake son sani wani shege ne ya yi kiran uwar yarinyar nan ya sanar mata kai tsaye har take son zagina?" Mama ta ce" Aa Hajia ba zata yarda ta zageki ba, kawai rai ne ya bace, ama komai zai wuce , ita Allah ya bata lafiya, wanda ya hadasa haka kuma Allah ya bashi ribar da ta dace da shi" Sunna tattaunawar nan har suka isa gida A asibiti kuwa hajia nawarah basu tashi bada hakuri mai kama da zigi ba sai da aka watse aka barsu da Maman Yumnah Hajia Fatahiya ta saba yarta a kafada tana fadin" Zamu tafi Hajia, kin san mijin Yumnar bai cika lalaba abu ba, du girmanmu da matsayinmu na matan mahaifinsa in ya dawo ya same mu a nan yana iya zazaginmu , kin san abu da baban gida , Allah dai ya sanyaya ama ai abin ba tausayi sam, yarinya karama a hada da wannan ina zata saka ranta, yaya zata iya kishi da wannan mace, ai kawai in nice Elhajin zan nemi gani a duba lamarin nan , gaskiya a zaba y'ata ko wancen kaska rabi mai jinni jikar" Hajia nawarah ta cafke da fadin" Uhum, Ni dama na san a irin kwadayin yarinyar nan da iyayenta komaima zai faru, Allah dai ya sa a barwa Yumnah cikinta kar aje a kaita wajen bokaye a rabata da cikinma dan kuwa na tabata kai sake Elhaji ba zai aurawa Magidanci wannan guzumar ba, menene abin mora a mota mai hayaki? Wahala ce kawai, Allah dai ya kyauta mun tafi kar ya dawo ya wulakantamu , kin san bashi da sauki ko kadan!" Sosai abin ya sake rikita mata lisafi, suka fice suka barta zaune ta zubawa waje daya ido har Akilah ta dawo ta zauna gefenta kanta a kasa ta kasa cewa komai ama tana sauraron wayar mahaifiyar Tata domin ta yi kiran babansu ta sanar masa abinda yake faruwa ya kuma ce zai kirayeta yanzu yanzu su koma gida zai dawo shima yanzun ya sameta Huci ta sauke tana share hawayen fuskarta ta ce" Innalilahi Wa inna ilaihi raj'une, kar dai idonmu ya rufe mun biyewa Yumnah da son da take yiwa yaron nan mun aura mata marar mutuncin dan kasuwa? Ki duba ki ga kaf dinmu ya kora ba jin nauyina yace zai kawo min y'ata kennan yana iya sakinta ba damuwarsa bace ko?, Kin kuwa ji me iyayensa ke fadi? Wai bari su yi su koma kar ya dawo ya same su ya wulakantasu, wai ya saba, to ya wulakanta su su, Ni wacece da ba zai min ba? Uwa uba y'ata? Innalilahi Wa ina ilaihi raj'une kar dai mun shigo rigimar da ta fi karfinmu, d'an baba da so ne ubansa ya masa aure ko shekara y'ata bata rufa ba a gidansa ba shawara ba komai kuma kakarsa ta zageni tasss? Ba zai yiwu ba, Allah ba zan iya yarda ba, sai an saki yarinyar nan ba za'a hadata kishi da Yumnah ba, ko ni uwarta ba'a min kishiya ba bale ita!" Ita dai Akilah kanta a kasa, har ta gama kira ya shigo wayarta mahaifinsu bai tsaya sauraronta ba ya bata umarnin kasancewa a gida yanzu yanzu yana jiranta Da kyar ta yarda suka tafi tare gidan suka bar Yumnar a asibitin, a gaban idonsu Nurse ta shiga da kayan kula da ita da komai , itace mai jinyarta kuma likitocin sai lekowa suke ana fadin matar docter ce ba lafiya, ita ya san za'a kula da Yumnar fiye da du inda zasu kaita, fatanta mahaifinta ya ci karfin wannan fitinar dan babu inda zata kai su sai dana sani Sosai ya samu hutun shima a asibitin a ranar, barcin da bai samu ba jiya ya samu ya dan rama sannan ya sauka ya koma dakin Yumnah ya dubata sosai da karin ruwan da aka jona mata da abinda aka rubuta za'a ringa mata har ta warware sannan ya yiwa nurse din dake tare da ita salama ya nufi gida Ko da ya isa gidan part dinsa ya wuce ya shige wanka, Yana gamawa ya je wajen mahaifiyarsa ya zauna suka dan taba fira sannan ya je wajen mahaifinsa, daga nan ya yi tafiyarsa bangarensa ya kwonta dan zai je aiki ne goben da wuri dole Washe gari karfe takwas da yan mintina Sauri take yi tamkar zata zura da gudu sakamakon yan mintinan da ta dora a yadda ta saba zuwa asibitin, a cen kasan zuciyarta kuwa fada take yi kamar zata ari baki na irin tsayar da Itan da direban ya yi da irin yadda Mama da kanta ta sakata saka wannan suturar ta jikinta kuma ta rufeta da fadan wai ta saka turare da yawa bayan yanzu matar aure take, ita abinma ya so bata dariya, ama kuma da ta duba tsantsareren kunshin hannayenta sai ta ji wani dadi dan kunshin ba karya ya zanu Allah ma kuwa Da dan gudu kadan cike da tsoron kar sabon takalmin nata ya kayar da ita ta saka hannunta ta hanna lft din rufewa sannan ta shige da sauri tana dan haki a hankali tana duban mutanen ciki ta furta" Barka da safia" Docter Aliyu , da sister Bahija ne suka amsa, Sister Bahijar na rike da wata yar akwati baka a hannunta tana duban Khausar sunna dan jiran ta danna wajen da zata sauka dan ya rufe su tafi ta ce" Dubiya kika zo ne? A wani etage zaki sauka ne? Yi ki danna muna tare da Sir muma bangaren dubiyar muka nufa" A hankali ta ji gabanta na neman yankewa ya yi faduwar da bata taɓa ji ba, sakamakon mutumen dake tsaye ya bada baya ya dan juyo , ashe waya ce yake amsawa , fuskar nan tasa cike da kamilalan saje, bakinsa dan ciwat da shi, idannuwansa dauke da farin tabarau, rigar jikinsa baka ce sidik sai abin wuyansa ruwan kasa mai duhu, ama rigar da wani tsabar sabon salo da rashin jin magana boturanta uku reras a bude suke, da hannunsa daya yana dan alamun balawa yake yi, watau ya fito ya ratso doguwar tafiyar nan bai Bala ba sai a nan, hannun dake rike da wayar kuwa agogo ce shekekiya dai Wali take irin na rashin mutuncin nan Wada ke nuna wanke hannunka ka taba ne ya wani kafeta da duban da ta tabata shima bai zaci ganninta ba da bai dubeta ba dan abin kunyar da aka launa masu su , wai su din nan Da karfi KHausar ta juya bayan ta zarro ido jikinta na rawa ta saka kafa ta fita daga lft din da gudun balaki ta saki yar wayar salular Tata a nan da rigarta ta Nurse ta karasa bakin matatakalar hawa ta zauna tana haki zuciyarta tamkar zata buga da tashin hankali A hankali ya lumshe idannuwansa, ya dan girgiza kansa da idannuwansa ya yiwa docter alamun ya rufe su tafi, sannan ba nuna kyankyami ko wani abin ya duba ya dauki wayar nan da rigar daidai abin ya tsaya ya fice gaba sunna biye da shi ya yiwa sister Bahija shiru a lokacin da take tambayarsa ya bata kayan ta rike, dama kayansa ne a hannunta, ama ya yi kamar kurma yake ya bude dakin da Yumnah take ya shige A bangaren Khausar kuwa hannaye ta saka ta talabe tana jin tsararen kukan dake neman zuwar mata Innalilahi Wa inna ilaihi raj'une, yanzu itace take tsoron kallon besty? Ita da ta zo da kudirin su hadu ta sanar masa su fa samawa kansu mafita tun wuri? Shin yaya zata fara masa zancen nan ne? Ta tabata shima abin ya wuce tunaninsa, ina ita ina shi? Me zata ce masa ne? Kai bari ta mike ta je ta yi jiransa kofar office dinsa su zanta, ya bata takardarta ta koma ta kaima Aba, wannan magana ta Aba cewar a zauna da wahala Bama zata iya zaunawar ba gaskiya Tana mikewa ta ji ana fadin"....... ☹️☹️☹️☹️🙃🙃🙃🙃🙃🙃🙃 💔💔💔💔❤‍🩹❤‍🩹💔💔💔💔 *DA CIWO A ZUCIYATA* 💔💔💔💔❤‍🩹❤‍🩹💔💔💔💔 _MALLAKIN_ *SAJIDA NIJAR* *FREE BOOK NE* 4️⃣5️⃣ *GARABASA, GARABASA, PROMOTION, PROMOTION DIN LITATAFAN MARUBUCIYAR A KAN FARASHI MAI SAUKI 1K, YAN NIJAR KUWA 1000 FRANCS CEFA* 1: Duk karyar kada 2: Yar mahaukaciya 3: Neman na kaina 4: Bani da zabi 5: Bak'a ce 6: Kutkale 7: Makauniya ce 8: Mage 9: Duk nisan jifa 10: Idan ka raina inda kake 11: Dutse 12: Alkalamin kadarata 13: Bani da zabi 14: Dakika Biyar 15:Wata kokowar 16: Aure yakin mata 17: Ni zan ladabi 18: Daga tafia daukar soja *Dukansu a kan farashi mai sauki, zaka saka dubu guda ne domin promotion ne nake yi, ka tuntubeni kan layina kamar haka +227 93 81 16 18, Sajida Nijar* Now *Da CIWO A ZUCIYATA* *Tallah, tallah, tallah* *SECRET DE LA FEMME DU MANGA* _Gidan Kamshi, Sirrin Manyan Mata, nesa tazo kusa,Amarya ,Uwar gida,Ango da mai gida Har ma da yan mata da samari shin kuna sane da cewa HAJIYA FUSAM ta shirya tsaf domin gwangwaje ku da turarakunta masu dankaran kamshi? Tare Kayan gyaram jiki na musamman ,wanda daga nesa kamshin ki kadai ya wadatar ya isar da sakon zuwanki waje,gidan ki kuwa sai ya zam abun kwatance wajen kamshi, kar na cika ku da surutu bara in fara zayyano su_ Farar Humura Bakar Humura Humura special, humura de bain Humura epicé Lait de nuit Parfums désodorisant Parfums rideau et dras Lait de nuit Alkam Kulakcam *Waɗannan kadan ne daga bangaren turaran ruwa* Gagab, sandal flex, Durot, durus, sandal fleur, tafarce, farce, sandal bangui, sandal, hypotonic sandal, al'ut, coktail creation VIP, Gajiji, Mankaji, turaran wutar labule da cafet, Aba malan, boulettes *Munada bangaren gyaran jiki kamar haka:* mai mai saka santsin jiki, mai mai kanshi, Kayan gyaran jiki mai saka fata ta yi santsi da laushi, kayan gyaran jiki mai saka fata ta yi fari, Sabulu mai saka fata ta yi haske, sabulu mai saka fata ta yi santsi, sabulu mai goge yanayin fata, mai wanda baya saka fari mai gyara fata Sayen na gari mai da kudi gida,sai an gwada akan san na kwarai💃💃 Hajiya Fusam na zaune a kasar Niger domin yin magana da ita kai tsaye tuntuɓi wannan number 97 82 44 94 *SECRET DE LA FEMME DU MANGA* Gidan Kamshi, Sirrin Manyan Mata💃💃💃💃💃 Ta ce" Khausar Muktar? Alhamdulilah, zo maza kama wannan ki hau cen dakunan VIP ki jona mata wannan allurar, yi gagawa zan kai hoton cikin da akai mata ne waje Docter tana jirana, kar sai na je na jona mata ruwan kuma ran sir ya bace" Magana take yi da dan gagawa da alamun azalzala , sai kuma ta dan dakata tana kallon KHausar din Da dan mamaki ta ce" Ke wai lafiya? Ina rigarki da takalmin ki na aiki? Ko dubiya kika zo yau?" Da sauri Khausar ta girgiza kanta tana kama kanta ta ce" Aa aunty kayan na bari a adaidaita sahu shine nake jira a kawo min" Kai ta dafe, sai kuma da dan sauri ta cire Tata farar rigar tana mika mata ta ce" Saka bani abayar nan ki je ki yi aikin nan Ni inada wata a office dina in an kawo maki taki kya kawo min" Tana fada ne tana taya Khausar cire abayar jikinta, da sauri Khausar ta dora rigar auntyn tasu ta tare kwanon silbar mai dauke da maganin ta sakarwa auntynsu abayar da ta ɗora saman riga da sket dinta sababi masu masifar kyau wa'inda suka kama jikinta dasss da su Juyawa ta yi ta koma lft din tana adu'ar Allah ya sa har ta gama ta koma kar su hadu da shi, ta fi ganewa ta tarda shi da kanta Lft din na tsayawa ta fito a nutse ta nufi VIP na dakunan ma'aikatan asibitin a ranta tana tunanin waye ba lafiya a cikin ma'aikatan asibitin, dan kuwa waje ne da ake saka manyansu ko ahalin manyansu Tana daf da karasawa dakin ta dubi madubin dake ajiye sai walwali yake Gabanta sai da ya yanke ya fadi, a dan rikice take kallon kanta tun daga sama har kasa, Watau dama aunty ba wani tsayi ne da ita ba, kuma tana da jiki hakan ya sa rigar Tata ta shigi Khausar, sai dai ta je cen daidai da dima diman cinyoyinta ta wani hau take budewa idan tana tafiya A raunane Khausar ta hadiye yawu mai wahala tana jin nauyin shigar Tata, da dan sauri ta karasa kofar dakin ta ayana magana kamar haka' zan shiga in yiwa marar lafiyan allurar sai in koma gida, idan na je sai in dauki wayar Baba in kirashi mu yi magana kawai, sai ya zo mu daidaita ya bani takardar kawai' A nutse ta bude dakin bayan ta dan buga kadan sannan ta yi salama kasa kasa sosai, dan wannan din shine dabi'arta, koda tana likita tana kiyaye hakin mutane, bata cika irin shigowar nan kai tsaye fuska daure ba ta wasu likitocin, takan dan buga ta dan yi jim, sannan ta bude ta shiga da sallama a hankali duda ta san nurse zata tarar sai marar lafiyar dan kuwa yanzun ba lokacin shigowa gannin mararsa lafiya bane, sai an jima kusan sha biyu na rana ake budewa a bada damar ziyara, karfe uku kuma a rufe sai shigar sasafe karfe shida zuwa takwas rufe A hankali ta ja ta tsaya idannuwanta suka sauka a kan fuskarsa da kuma wace ke kwonce tamkar babu rai a jikinta, ga dukkan alamu barci ne take yi mai nauyin gaske A hankali Khausar ta lumshe idannuwanta gannin shi bashi da niyar kautar da nasa duban a kanta, kamar yadda ya saba a da cen, a kanta yakan dan jima yana kallonta , sai dai a da din bata dauki haka a bakin komai ba, yanzu kuwa sai take gannin hakan bai dace ba A hankali ya dan yi gyaran murya ya mike daga saman kujerar da hannunsa ya mata alamun ta yi aikinta sannan ya koma bayanta sosai ya tsaya ya dauke kansa a kanta dan ya san wacece ita, bale sabon yannayin da ya ga ta ara tsaf take iya juyawa ba tare da ta yi aikin da ya kawota ba Jiki ba karfi ta ajiye kwanon, sannan ta duka ta tsayar da gudun karin ruwan, ta daidaita allurar da ruwanta ta bude wajen da aka jona karin ruwan a hankali ta rike tsintsiyar hannun Yumnar ta shiga zuba mata ruwan allurar a hankali a hankali tana dan duba yannayinta domin allura ce mai zafi ba'a zugata zuuuuuuu ta tafi, kuma tana iya taba numfashin mutun ko ta saka shi amai ko muguwar juwa shi yasa ake yi a hankali ana hankalce da motsin mutun Sai da ta gama saka mata ruwan allurar sannan ta maida mata karin ruwan A hankali ta juya tana dan duba dakin dan gannin abin auna bugun zuciya Dayan nan dai na wuyansa shine, ita kuma nata yana cikin rigarta da ta yar a cikin lft Ajiyar zuciya ta sauke bayan ta karfafawa kanta gwuiwa cewar Besty ne fa, TAUFEEK ne fa, dilla menene a ciki Ba tare da ta sake saka tsoro ba ta nufe shi tana aro jarumta tana yafawa kanta ta ce" Shin me yake damun Yumnah ne? Ban san bata da lafiya ba, dan bani abin nan na ga bugun zuciyarta" Maimakun ya bata abinda take nuna masan sai kawai ya kama hannunta kiiiii ya fice da ita daga dakin Jefa kafa take yi gabanta na faduwa domin bata san ina suka nufa ba, kuma irin yadda fuskarsa ta dauki ja alamun ransa a bace ko menene sai ta sake tsorata ainun har suka shiga lft suka sake hawa sama cen wajen office dinsa Ko da lft din ya tsaya hannun nata ya cika ya yi gaba yana kunce abinda ke daure a jikin rigarsa na wuyansa dan ji yake yi tamkar zai tsaida masa numfashinsa ya dadana code din kofar office dinsa ya shige lokaci daya ya dauki commande din camarar bangarensu ya sakata a halin duhu sannan ya kurawa kofar ido yana jiran shigowar ta KHAUSAR da ta gama summa a tsaye da kyar ta cira kafarta ta karasa office din Rana shigowa ta ajiye farar rigar aikin domin itama du a rikice cire rigar ta yi ta tunkaro kusa da table din da yake tsaye kanta tsaye tana dubansa idannuwanta na cikowa da kwallah ta ce" Kana tunanin laifina ne?, TAUFEEK kana tunanin nice na saka su Aba aikata aikin nan?, Walahi walahi ban sani ba, nima na san ai na wani hadi, in kana tune ka min alkawarin kasancewa da Ni har a Daura aurena da .........." "Khausar Please cn U be quiet?!" TAUFEEK ya fada a kasashen da ya saka Khausar zuba masa ido tana jin tamkar zata kifa a tsayen da take , shin yaya zata kwatanta masa cewar ba fa ita tace a daura mata aure da shi ba? A nutse yana binta da kallo ya ce" sai yaushe zaki fara jin maganana ne? Menene wannan shigar? Ina hijab dinki? Me yasa kike son daukan dabi'ar da zata ringa bata min rai? Babu ruwanki a gaban kowa sai ki arta a guje ? Kina kallo muna tare da docter kika wani fita da gudu menene haka ne?" Da mamaki take kallonsa, sai kuma ta kalli jikinta A hankali ta shiga juyawa a gaban nasa har sai da ta juyo tana fuskantarsa a sanyaye ta ce" Menene laifin shigata? Me yasa kake son min fadan shigata ne bayan na san cewa harda ita a tsaikon samun mijina yanzu na kare da ......" Ta yi shiru sakamakon zuba mata jajayen idannuwansa da ya yi yana sauraronta Gannin ta yi shiru a hankali ya ce" Kika kare da me?" Khausar ta dafe gaban goshinta, a hankali ta ja kujera ta zauna sannan ta mika hannunta ta kama bayan hannunsa dake jimke saman table din a tausashe dayan hannun nata kuwa ta bude abinda ke ajiye ta ciro tisu fari ta nufi gaban goshinta da shi a hankali tana share zufar da ta karyo mata kasa kasa ta ce" Dan Allah ka zauna, ka san ba son rikici nake ba, kuma baka san abinda ya faru ba ga dukkan alamu, ka zauna dan ina tsoron in na fada maka yanzu ka fadi, Taufeek its vry srius , ka zauna Please" Hannunsa ya janye daga jikin nata, domin tunda ta dora din tana magana ne tana dan shafa bayan hannun nasa da sigar rarashi ba da wata manufa ba, wace sshi kuwa hakan ba daidai da yannayin da yake iya dauka bane Da ƙafarsa ya dan tura kujerar baya ya zauna yana kallonta , a hankalin da sam bata so yana mata magana ya ce" Kika kare da me? Tl me" "Na kare da auren aminina, abokina, freind dina, TAUFEEK basu fada maka aurena da aka daura da kai bane ko menene na ga ba maganar kake min yanzu ba?, TAUFEEK ka san cewa wai ashe Ni aka aura maka.....?" Ta fada tana watsa hannayenta hadi da dan zarro idannuwanta alamun ta fada masa tashin hankalin nan Bakinsa ya dan tabe yana kauda dubansa ya ce" Eh haka na ji" Khausar ta girgiza kai ta ce" Ka ji? Kennan ka ji? Ya Allah, da ka san irin yadda na yi ɓaci a kwana biyun nan da ka sha mamaki, TAUFEEK aminina?" TAUFEEK ya zuba mata ido, ya dora hannayensa duka biyu yana dubanta ya ce" Eh, sai aka yi yaya?" "ka kuwa ji me nace ne?" Khausar ta fada tana dubansa TAUFEEK ya dan dantse lebensa da dan jin yana daf da kowa a wannan dogon maganar da tarin raini ke jagoranta tsakaninsa da Khausar ya ce" Eh na ji me kika ce, an daura maki aure da Ni, Ni amininki, nace eh sai mene kuma?" Baki da ido da hanci ta bude tana kallonsa har ya mike ya nufi wajen frij din office din nasa ya ciro faro ya bude ya sha ya ajiye sauran cikin abin zuba shara dan bai shanye ba wanda ya rage din kuma kadan ne Ya karasa ya dauki suturarsa kala blu mai haske wando da riga irin na likitoci wa'inda yake shiga dakin tiyata da su ya bale boturan rigar jikinsa ya cire rigar A zabure Khausar ta mike tana kawar da kanta, sai kuma ta koma ta zauna ta sada kan nata tana dadana yatsunta tana addu'a kunnayenta na jiyo mata motsinsa alamun harta wandon a nan TAUFEEK ya saka har ta daina ji idannuwanta a rintse zufa na neman karyo mata sai kuma ta ji maganarsa daf da ita , a kamilance harufan bakinsa ke fitowa yana dubanta ya ce" igiyoyin aurena uku ke wuyanki, ina fatan zaki kula ba tare da kin takura min tabatuwarsu a kanki ba!, Ki kula na kasance mai jinkiri sosai, inada hakuri sosai, ama a kanki babu abinda bai sameni ba......Please Khausar ki dan sanyaya mana tafiyar , ko ba komai kin ce auren hadi ne, shi kuma ai sai an zauna shi ko? Kin dai san Ni ba marar kunyar da zan cewa su Aba wai yanzu yanzu zan bijire masu bane, in ke wuyanki ya rika ki je ki fada masu kawai sai a duba a ga abinda ya dace a yi......., Khausar My wife......... A dan zabure ta dago ta zuba masa ido TAUFEEK ya dan dantse lebensa kadan ya ce" my wife bata da lafiya, kin san ciki ne da ita, kuma ina tsoron laifinki ne....... ki dan yi zamanki a nan har a tashi kin ji?" Yana gama fada ya saka hular a kansa ya dauki glasss dinsa ya mayar ya ajiye mata iphone dinsa a gabanta sannan ya wuce a office din, du a kokarinsa kar a fahimci irin takaicin da ta shaka masa, da kuma tunanin mema take nufi ne yarinyar nan da shi har ya karasa dakin tiyatar da ake daf da yiwa marar lafiyan allurar kashe jiki gaba daya a saka shi a duniyar barci dan aiki ne zasu masa su ciro masa ciwon kansar dake kansa Bayan fitarsa Khausar ta jima tana kallon hanyar da TAUFEEK ya fice, dan yana fita ya mayar da kofar ya rufe wanda ke tabatar mata cewar sai kuma ya bude da kansa koda zata iya fita A tsorace ta maido dubanta kan hotonsa da yake matsayin zane a jikin garu ta zuba masa ido kirjinta na sama yana kasa A birkice take tambayar kanta *ME KENNAN?* OHO☹️ *Promotion dinmu dai ana Tata yi, ana ta karba, ana ta yi, yauwa da 1k dinki za'a baki baki daya nvls DINA yar uwa, garzayo ki amshi naki ki more in sha Allah,😍😍😍😍😍😍😍💓💓💓💓💓💓💓🙃🙃🙃* 💔💔💔💔❤‍🩹❤‍🩹💔💔💔💔 *DA CIWO A ZUCIYATA* 💔💔💔💔❤‍🩹❤‍🩹💔💔💔💔 _MALLAKIN_ *SAJIDA NIJAR* *FREE BOOK NE* 4️⃣6️⃣ *GARABASA, GARABASA, PROMOTION, PROMOTION DIN LITATAFAN MARUBUCIYAR A KAN FARASHI MAI SAUKI 1K, YAN NIJAR KUWA 1000 FRANCS CEFA* 1: Duk karyar kada 2: Yar mahaukaciya 3: Neman na kaina 4: Bani da zabi 5: Bak'a ce 6: Kutkale 7: Makauniya ce 8: Mage 9: Duk nisan jifa 10: Idan ka raina inda kake 11: Dutse 12: Alkalamin kadarata 13: Bani da zabi 14: Dakika Biyar 15:Wata kokowar 16: Aure yakin mata 17: Ni zan ladabi 18: Daga tafia daukar soja *Dukansu a kan farashi mai sauki, zaka saka dubu guda ne domin promotion ne nake yi, ka tuntubeni kan layina kamar haka +227 93 81 16 18, Sajida Nijar* Now *Da CIWO A ZUCIYATA* *Tallah, tallah, tallah* *SECRET DE LA FEMME DU MANGA* _Gidan Kamshi, Sirrin Manyan Mata, nesa tazo kusa,Amarya ,Uwar gida,Ango da mai gida Har ma da yan mata da samari shin kuna sane da cewa HAJIYA FUSAM ta shirya tsaf domin gwangwaje ku da turarakunta masu dankaran kamshi? Tare Kayan gyaram jiki na musamman ,wanda daga nesa kamshin ki kadai ya wadatar ya isar da sakon zuwanki waje,gidan ki kuwa sai ya zam abun kwatance wajen kamshi, kar na cika ku da surutu bara in fara zayyano su_ Farar Humura Bakar Humura Humura special, humura de bain Humura epicé Lait de nuit Parfums désodorisant Parfums rideau et dras Lait de nuit Alkam Kulakcam *Waɗannan kadan ne daga bangaren turaran ruwa* Gagab, sandal flex, Durot, durus, sandal fleur, tafarce, farce, sandal bangui, sandal, hypotonic sandal, al'ut, coktail creation VIP, Gajiji, Mankaji, turaran wutar labule da cafet, Aba malan, boulettes *Munada bangaren gyaran jiki kamar haka:* mai mai saka santsin jiki, mai mai kanshi, Kayan gyaran jiki mai saka fata ta yi santsi da laushi, kayan gyaran jiki mai saka fata ta yi fari, Sabulu mai saka fata ta yi haske, sabulu mai saka fata ta yi santsi, sabulu mai goge yanayin fata, mai wanda baya saka fari mai gyara fata Sayen na gari mai da kudi gida,sai an gwada akan san na kwarai💃💃 Hajiya Fusam na zaune a kasar Niger domin yin magana da ita kai tsaye tuntuɓi wannan number 97 82 44 94 *SECRET DE LA FEMME DU MANGA* Gidan Kamshi, Sirrin Manyan Mata💃💃💃💃💃 ' Matarsa bata da lafiya, cikine da ita? Wauh, masha ALLAH , to ama me yake nufi da yana tsoron Laifina ne? Bayan wannan a kan me zai rufeni ya yi tafiyarsa? Me yasa wai ya cika takura min da shigata bayan ina shigar kirki? Walahi TAUFEEK yana da damuwa, me yasa ya cika haka ne? Ni ga abinda nake nuna masa' Kasancewar wayar da ya ajiye mata ba wani damunta ta yi ba, batama san yaya zata yi aiki da ita ba sai ta bar masa abinsa nan saman table din ta koma saman cafet ta zauna tana ta tunanin rayuwa da abinda ke zagaye da ita, tun tana iya rike yinwar dake kwakular hanjinta har ta ji kuwa na dibanta, a hankali ta silale ta yi kwonce ta yi matashi da hannunta tana lumshe idannuwanta da Adu'ar Allah ya sa aikin da zai yi ba mai daukan lokaci bane A kala sun dauki awa bakwai, dan tun karfe tara na safe sai hudu da rabi na yama kunnayenta suka ringa tsinkayo mata alamun bude office din A hankali ta bude idannuwanta da suka fada ta bi takun sawayensa da kallo har zuwa hannunsa mai dauke da wasu manyan ledoji biyu Idannuwanta ne suka hango mata saukar rigarsa da sauri ta maida idannuwan nata ta rufe ta juya ta bada baya tana Turo baki cike da haushi da takaici Sai da ya maida kayansa sannan ya dauko ledar mai abincin ya karaso inda take kwoncen nan a Nutse ya zuba mata ido "Sai na tsumata iya tsumi, sai na bata tsumi ta yadda du wanda ya dauka zai san ya dauki mata, sai na......" Da sauri ya cire kansa a wajen da idannuwansa suka sauka yana a'uziya a kasan zuciyarsa sakamakon tuno magangannun HAJIA a lokacin da take bayanin KHausar din A hankali ya ce" Tashi mana kin fa san na shigo ko?" KHausar ta sake hade baki tana ji inama zata iya jan mahaukacin tsaki jama'a ko zai fahimci kololuwar bacin ran da take ciki, sai dai ta san ko firar arziki suke baya son tsaki , dan haka ta masa banza tana tunanin ta yadda zata iya mikewa ta je ta samu dan abin sakawa bakarta dan tana kyautata zaton tsaf take iya faduwa idan ta mike tsaye Murmushi ya saki ya yi zaune , irin zaman nan na mike kafa, hankali kwonce ya fitar da manyan kwalayan pizza din da docter ta amso masa ya ajiye da jusss masu dadi ya ajiye , hankali kwonce ya bude guda , kanshin abin kaicop din da naman kazar nan da nan suka je hancinta, ba wata damuwa a tare da shi sai tarin sakewa kamar yadda ya saba, idan har yana tare da ita a inda take yana iya zama koda kuwa a dandar kasa ne ba tare da ya share wajen ya ko damu ba, shi dai tun bai iya cin awara da dambu ba itace ta koya masa kuma a leda a daure na arba'in da tarin yaji da mai, tun idan ya dandana yajin na goge masa lebe har ya zama ɗan gari ya iya ci hankali kwonce, a yanzu haka yana fitowa kafin a fitar da wanda aka yiwa aikin ya da docter ta amso abinci, aiki yake yi ama ya san cikin Khausara na cen yana kugi Hankali kwonce ya saka yar wukar ya fitar da gefe guda ya dauko a hannunsa ya dan sake yin wajen fuskarta da shi kanshin ya shigi hancinta da kyau sannan ya janye ya kai bakinsa ya cira yana lumshe ido da gangan kasa kasa ya furta" Dadihhhhh" A zabure ta dago kanta , tun tana Hanna kanta juyowa har ta mike zaune idannuwanta a kan hannunsa da kuma kwalin pizzar A hankali ta samu kanta da hadiyar yawu tana kallonsa , ta ga ya sake saka yar wukar ya yanko wani dan mitsil ta kai bakinsa A hankali ta gyara zama ta tana kallon dayan kwalin, sai kuma ta kalle shi tana kai hannunta wajen kwalin Murya a raunane ainun ta ce" TAUFEEK wancen nawa ne?" Hannun nata ya riko ya dage daga saman kwalin kafin ya girgiza kai , na hannun nasa da ya ciro ya kawo wajen bakinta da shi yana kallonta ya ce" Wannan ne naki" Pizzar ta karewa kallo, karama ce fa, to wannan ai ba haka take loma ba ita, ama kuma gudun kar ya cinye abinsa sai ta budi bakin ta amsa Dan murmushi ya saki yana sake binta da kallo ya ciro wani irin wancen Wannan karon ido ta zubawa pizzar sai kuma ta shiga takwaf takwaf da fuskarta ta Ce" TAUFEEK, ban fa karya ba na zo, kuma yanzu karfe biyar , dan Allah bani wancen din ko in je in samo wani abin in ci ni dai" A ransa yake dariyarsa, dama ya san da wahala fushin ya yi nisa, dan haka ya miko mata Hankali kwonce ta bude ta saki wani murmushi kafin ta mika hannu ta dauko jus din ta ta gyara zama a Nutse ta shiga cin abinta tana jin ruwan jikinta na dawowa, sai da ta kusa rabi ta dago dan yi masa maganar da ta fado mata a ranta, sai ta ga ita yake kallo da kwalbar jus dinsa a hannunsa, shi baima wani ci da yawa ba ya tsaya yana Binta da kallo A hankali ta dan dauke kanta kasa kasa ta ce" Wai me yasa yanzu kake son daukan dabi'ar kallo bayan ba dabi'arka bace?" Shiru ya yi mata, maimakun ya dauke duban nasa sai yake dan basarwa ama kuma yana sake dubanta Gaba daya ta ji ta shiga hali na takura da wannan yannayi Baki ta Turo ta dago ta zuba masa ido ta ce" Wai MEYE wai? Ni fa Bana son kallo ka fi kowa sani, kaima ai Inaga abinda ke cikin tsarinka ba kallo Ni ka daina kallona" Murmushi ya yi ido cikin ido ya ce" Ina kiyaye duban abinda yake haramun a Wajena ne ai KHAUSAR" Sai da ta ji tamkar ya gwaura mata mari ne Da sauri ta so juya idannuwanta dan jin abin na neman fin karfinta, sai dai ta kasa tana kallonsa ta ce" Me yasa kake sha'awar gannin ka dagan hankali ne? Bama wannan ba MEYE yake damun Yumnah kace laifina ne? Kuma TAUFEEK dan Allah mu daidaita yadda zamu fuskanci su Aba kan maganar nan ka ji?" Sai yanzu ya dauke dubansa a kanta, maimakun ya bata amsar tambayoyin nan sai ya mika hannu ya janyo dayar ledar ya bude yana ciro wani yadi mai nuni da hijab ne manya biyu, milk da baki Bakin ya miko mata yana fadin" kin kuwa san wannan zai fi maki kyau?" Hijab din ta amsa bayan ta tura wata pizzar a bakinta ta goge abin fulawar kadan ta bude hijab din tana kallonsa sannan ta dago tana kallon TAUFEEK din ta ce" Na MEYE wannan?" TAUFEEK ya ce" Naki ne, na zuwa aiki " KHausar ta tabe baki ta nade ta ajiye masa a gabansa ta ce" Ka ga Ni na kurce fita da ire irin Wadinnan ko aure na yi, dan rufe jiki ai ba dole sai da hijab ba, Larabawa hijab irin namu suke sakawa ne? Abaya ce da nikaf" "Auren banda wanda aka miki yau kwana biyu?, Kuma larabawa kika ce, mu a nan ai sai da wannan ko KHausar?" Ya fada a tausashen da ya saba idan sunna musu KHausar ta tsatsareshi da ido, sai kawai idannuwan nata suka fara cika da kwallah, gata dama da saurin zubo da su a gabansa, dan bata iya rike rauninta in dai a gabansa take Muryata na neman shakewa hawayen na balewa tana dubansa ta ce" kai ba ruwanka da lokacin tsokana da lokacin da ba na tsokana ba, babu ruwanka TAUFEEK, haba dan Allah yaya ina maka tambaya kana jina ama sai ka ringa zagayewa? Dan Allah ka bani amsa"..... TAUFEEK ya dan dantse lebensa, hakan yannayinsa ne na rike kansa idan abu na neman daga masa hankali A Nutse ya fuskanceta ya ce" Rashin lafiyar matata tace na zaba ko ke ko ita shi yasa take kwoncen" Ido ta zarro tana dafe kirji ta ce" Innalilahi Wa inna ilaihi raj'une, wayo ba shiga uku yarinyar nan ta ji wannan abin? Dama ta fara min abubuwa na raini ai yanzu sai ta yi da huja, dan Allah ina fata ka fada mata Bama za'a kai ga maganar zaba ba, itace uwar gida kuma amarya dan ko Ni ba zan bari ka mata kishiya ba!" Dan murmushi ne ya yi na gefen baki kadan sannan ya mike yana ajiye mata jus din a nan ko sha bai yi ba, dama ya bude zai fara sha ne ta fara magana sai ya dakata KHausar ta hade sauran pizzar tasa da Tata ta rufe ta mike tana daukan dan kwalin abayarta tana dubansa ta ce" TAUFEEK, yaya maganar yadda zamu fuskanci su......" Bata san cewa ta kure masa waje ba, batama san cewa sunna iya yin daf da daf ba, sai dai ganni ta yi ya juyo sunna kusa da junna sosai ya saka idannuwansa a cikin nata a kausashe ya ce" Wannan maganar itace ta karshe da zan nanata maki, Ni ba fitsarare bane, ba zan iya duban Baba da Aba na musu rashin kunya ba, idan na yi hakan ba zan hadu da rahamar Ubangiji ba, dan iyaye ne, ko wa suka bani Ni din mai biyayya ne koda bana so, idan har ke wuyanki ya isa yanka, babu ruwanki da abinda za'a ce, babu ruwanki da abinda Allah zai miki ki je ki bijire in sun bani umarnin YANKEWA zan yanke, ama a yanzu sunnanki *MRS TAUFEEK KHAUSAR*, bana son maido maganar, KHausar bana son rigima , ki dauki hijab ɗinki ki saka , kin ga wanda baya bin umarnin mijinsa wuta ce makomarsa ko?, Matata kuma zaki bata hakurin aurar mata miji da kika yi, ki je direbanki na jira ni sai na dauki Yumnah" "lah ha ila ha ilalahu Muhammadu rasululahi sallalahi alaihi Wa ahlihi wa salam, innalilahi wa inna ilaihi raj'une, lah lah wayo Allahna cikina , na shiga uku , Taufeek haba TAUFEEK, wayo allahna......" Dawurwura take yi, idannuwanta na marmarmar tana neman wajen da zata zauna, kamarma wace ke jin gudawa a irin yadda take son zagaye, haka kuma ta kasa kuma dago kanta bale ta Dube shi, tsoro ne? Kunya ce? Mamaki ne? Koma menene kalamansa sun hadasa mata wani irin abu mai girman da ya hannata sakewa ko ta sake dubansa A tsayen da yake binta yake yi da kallo har aka kuma neman izinin shigowa Allon tvn haska camarar ya kuma duba , ,kafin ya karasa wajen hijabin ya dauka ya karasa inda take tsaye ba tare da ya jira cewarta ba ya zura mata hijabin bayan ya janye dan kwalin A kaikaice ya dan bi wajen da ya fi komai birkita masa lissafi saboda rashin sirinsa a jikinta, kwarai ya ji haushinsa dan da hijab dinma ana ganninsa, ko dan hijab din mai rabar jiki ne irin hijaban yan matan zamani? Fuskar hijabin ya gyara mata sosai bayan ya rike fuskar da hannu daya ya zamo ta kasa kwacewa , sai kuma ya sauke dubansa a kan lebunnanta dake rawa rawa tana kallon fuskarsa da sajensa Dan murmushi ya yi, ya matse mata waje sosai ya rage amon muryarsa ainun ya ce" Kin san a kan shigar ki, ina iya toshe zuwa aikin nan, dan bana tunanin Akoy abinda zai iya daidaita bacin raina a kan hakan!" Magana besty ke yi iskar bakinsa na dokan leben KHausar jama'a Magana yake yi yana furuci kamar na yan giya jama'a Shin shi din nan ina kunyarsa ta je ne? TAUFEEK ne fa, kuma KHausar ce fa?😭😭😭kashhhhh Wannan bayanai sunne suka fi komai daga mata hankali har ya cika ta ya bude kofar docter ya shigo dauke da hoto da dukan bayanai ya gaishe da TAUFEEK sannan ya zauna ya shiga masa bayanin dukkan abinda suka gani a tare da Yumnah sannan ya tabbatar masa cewa sunna iya zuwa gida dan YANZUN ba risq na zubewar cikin 💔💔💔💔❤‍🩹❤‍🩹💔💔💔💔 *DA CIWO A ZUCIYATA* 💔💔💔💔❤‍🩹❤‍🩹💔💔💔💔 _MALLAKIN_ *SAJIDA NIJAR* *FREE BOOK NE* 4️⃣7️⃣ *GARABASA, GARABASA, PROMOTION, PROMOTION DIN LITATAFAN MARUBUCIYAR A KAN FARASHI MAI SAUKI 1K, YAN NIJAR KUWA 1000 FRANCS CEFA* 1: Duk karyar kada 2: Yar mahaukaciya 3: Neman na kaina 4: Bani da zabi 5: Bak'a ce 6: Kutkale 7: Makauniya ce 8: Mage 9: Duk nisan jifa 10: Idan ka raina inda kake 11: Dutse 12: Alkalamin kadarata 13: Bani da zabi 14: Dakika Biyar 15:Wata kokowar 16: Aure yakin mata 17: Ni zan ladabi 18: Daga tafia daukar soja *Dukansu a kan farashi mai sauki, zaka saka dubu guda ne domin promotion ne nake yi, ka tuntubeni kan layina kamar haka +227 93 81 16 18, Sajida Nijar* Now *Da CIWO A ZUCIYATA* *Tallah, tallah, tallah* *SECRET DE LA FEMME DU MANGA* _Gidan Kamshi, Sirrin Manyan Mata, nesa tazo kusa,Amarya ,Uwar gida,Ango da mai gida Har ma da yan mata da samari shin kuna sane da cewa HAJIYA FUSAM ta shirya tsaf domin gwangwaje ku da turarakunta masu dankaran kamshi? Tare Kayan gyaram jiki na musamman ,wanda daga nesa kamshin ki kadai ya wadatar ya isar da sakon zuwanki waje,gidan ki kuwa sai ya zam abun kwatance wajen kamshi, kar na cika ku da surutu bara in fara zayyano su_ Farar Humura Bakar Humura Humura special, humura de bain Humura epicé Lait de nuit Parfums désodorisant Parfums rideau et dras Lait de nuit Alkam Kulakcam *Waɗannan kadan ne daga bangaren turaran ruwa* Gagab, sandal flex, Durot, durus, sandal fleur, tafarce, farce, sandal bangui, sandal, hypotonic sandal, al'ut, coktail creation VIP, Gajiji, Mankaji, turaran wutar labule da cafet, Aba malan, boulettes *Munada bangaren gyaran jiki kamar haka:* mai mai saka santsin jiki, mai mai kanshi, Kayan gyaran jiki mai saka fata ta yi santsi da laushi, kayan gyaran jiki mai saka fata ta yi fari, Sabulu mai saka fata ta yi haske, sabulu mai saka fata ta yi santsi, sabulu mai goge yanayin fata, mai wanda baya saka fari mai gyara fata Sayen na gari mai da kudi gida,sai an gwada akan san na kwarai💃💃 Hajiya Fusam na zaune a kasar Niger domin yin magana da ita kai tsaye tuntuɓi wannan number 97 82 44 94 *SECRET DE LA FEMME DU MANGA* Gidan Kamshi, Sirrin Manyan Mata💃💃💃💃💃 Sai da ya gama masa bayani ya masa godiya sosai tamkar ba shine gaba da shi ba sannan ya tafi Yana tafiya KHausar ta karasa wajen da ta ga wayarta ta dauka ta juya ta nufi fita Har ta kama kofar ta juyo tana huci ta sake dubansa sannan ta fice hijab din yana yi kamar zai tadeta dan ya mata yawa fa Murmushi ya yi yana girgiza kansa, shi ya sa za'a sha rigima , bale irin yadda take tunanin ita ta haifi duniyar nan, ama ba komai Bara ya je gidan ya tarda wata rigimar kuma domin Mai kwanoni ya yi kiransa cewar ya yi kokari ya sauko da wuri Mahaifin Yumnah yace masa yana so zasu zauna Dan murmushi ya sake yi ya dauki abin bukatarsa ya yi kiran vigil dinsa ya zo ya kwashe ya kai mota, ciki harda sauran pizzar da KHausar ta rage, jus din ko sha bata yi ba, ya san ba koshi ta yi ba kawai ya daga mata hankali, kai shima baya jin magana sam..........😌 A lokacin da suka karaso gida tuni magariba ta kawo kai, hakan ya sa ya taimaka mata ta sauka sannan ya wuce masalaci Sai bayan sallar isha i suka dawo daga masallacin Direct bangarensa suka nufa da mahaifinsa, a ransa yana mamakin to wai a nan iyayen na Yumnar suke ne ko me? Mamaki bai idasa kamashi ba sai da suka shigo suka samu taron irin na asibiti, harda kishiyoyin Mama, wanda hakan ya matukar ba harta mai kwanoni mamaki, dan bai ga dalilin da za'a zo ana zama irin wannan a kan abinda ya isa da shi har ya yi yawa Zaman kansa kaure biyu suka tarar, su su HAJIA Fatahiya sunna bangare guda da su Yumnah da mahaifiyarta, ita kuma Mama tana zaune gefe daya da carbinta baki tana ja hankalinta a kan HAJIA dake magana daga cen cikin kicin TAUFEEK kam shi da kansa abin nan yana daf da saka shi nuna hali irin na fitsararu, Bama kamar yadda ya kula a tafiyar nan ana so ne a kawowa mahaifiyarsa raini, a shigeta ta inda aka san tana da karra da kawar da kai Bayan Salama bai karra komai ba sai ya karasa cen inda mahaifiyar tasa take zaune ya zauna a kasa daf da ƙafarta a hankali ya dan rabu kafarta kasa kasa ya ce" Matar mai kwanoni ina yini?" Mama ta yi murmushi, gannin HAJIA ta fito da kaskonta kato ta bada hantiti ta karaso ta mikawa maman tana fadin" Badeshi, hau da hawa'i, bakin duniya da saka ido, jarabar kishin matan uba da asiri ya komewa mai aikatawa dan ubansa, bade shi sosai Ni ba zai zauna da kyau ba" Mama kuwa ta amsa har yar dariya ta kubce mata gannin zaburar da ya yi ya zubawa HAJIA ido hade da hararan da ya saka ta kawar da kai kasa kasa ta ce" Da ubaanka kake!" A hankali Mama ta ce" Ka buda bakinka mana harda baki ko HAJIA?" HAJIA ta ce" Da so samu na yi in da ace daga Ni sai ke ne sai mun tube shi mu masa wankan magani , to a wajen nan harda haramunsa , bayan wannan Magidanci da aka masa yanka ai Ni ke goye shi , Ni din ba damuwa bane ama kin ga gaya irin ta bakin ciki to yau ko Ni ko du wani dan iska a wajen nan , a kan Magidanci babu abinda ba zan aikata ba!" A wajen wadda HAJIA take bakuwa a wajensa mahaifin Yumnah ne, shi kuwa tasa mahaifiyar ta rasu, tunda HAJIA ta fara magangannun nan ya samu kansa da jin wani irin girmanta a zuciyarsa, Walahi sai da ya ji yar kwala ta taru a idannuwansa, a ce kasan zuciyarsa kuwa sai yake ji inama inama ace tasa uwar ce yake kallo a haka, A sanyyaye ainun ya dubi mai kwanoni dake duban yannayinsa ya saki murmushi a hankali ya ce" Allah ya karra mata lafiya, Allah ya sa ka rabu lafiya da ita, Allah ya sa ta yi dace da kasancewa a aljana gobe kiyama" Mai Kwanoni ya yi murmushi sosai a hankalin shima ya ce" Amen ya Allah, Allah ya jikan HAJIA Laraba " Aban Yumnah ya amsa da amen Basu fara magana ba sai da aka gama turaren nan HAJIA ta dawo ta yi zaune a tsakiya saman kujera ta harde tana fadin" Kai zo daf da Ni" TAUFEEK ya yi tamkar bai jita ba, sai da Baba ya masa alamun ya je fa, sannan ya mike ya je ya zauna saman kujera kafadar HAJIA kafadarsa, HAJIA ta wani riko hannunsa kasa kasa ta ce" In suka ce a basu takarda in baka basu ba ina iya daga maka nono" Kasa kasan ya sake harararta ya ce" Tabas ta tabbata sai na maki aure a Saudiya, ki daga mana haihuwata kika yi yo?" HAJIA ta masa zuru sai kuma ta cika hannun tana cika tana batsewa ta ce" Na ga ubanda zai Hanna a saki wancen laujen, iskancin banza da wofi" Shi dai ya kyaleta yana sauraron salamar da mahaifinsa ya sake yi kafin ya ce" Elhaji Abdullahi ne ya nemi a yi zaman nan, a sanina na gayyaci HAJIA da mahaifiyar TAUFEEK ne, me yasa taron nan ya taru har haka?" HAJIA marwa ta dauke kai a ranta tana ayana' sai dai ku yi du abinda za'a yi a wajen nan sai an yi shi da mu!' HAJIA baba ta ce" Barsu, barsu ai ba komai, su zauna , ina son du wani makiyin ya ringa gannin ci gabansa a gaban idannuwansa, ku sani in har dayarku ce ta hadasa fitina kun yi aikin banza, Magidanci sai ya jera hudu sai dai a yi abinda za'a yi" Yumnah dake kwonce jikin adarta harara tamkar idannuwanta zasu fita daga jikinta, a ranta kuwa addu'a take yi Allah ya karbi HAJIA KOWAMA ya huta, dan bata tunanin in har HAJIA na kusa zata bari su rayu cikin Salama ita da mijinta Mahaifin Yumnah ya fitar da iskar bakinsa, a tausashe sosai ya ce" A yi hakuri HAJIA, a yi hakuri, Ni dama na nemi zaman nan ne dan na bada hakuri, domin ban san iya girman abinda mahaifiyar Yaren nan ta aikata ba, sai dai kamar yadda kika sani wani lokacin mata kan yi gaban kansu su manta du wani girma da ALKHAIRI su aikata aiki irin na son zuciya, Aure babu inda zai je, wannan yarinya Allah ya kadarta matar Elhaji ce, babu mai raba auren nan sai in Allah ne ya hukunta, in banda son kai irin nata da ace Tata ce aka aura zata so a maishe mata ita karamar bazawara?....." "Elhaji, Walahi, Walahi Walahi da a mata irin wannan auren gwara ace ba'a yi ba ka ji na rantse, nawa take ne Yumnar? Gata da yaron ciki, ba'a duba halin da take iya shiga ba shikennan sai ace an mata kishiya ko sanar mata ba'a yi ba?, To Walahi in saki take so a sakar min y'ata cen ya karata da uwar matan!" Mahaifiyar Yumnah ta fada tana fashewa da kuka tana duban mijinta, wanda ya yi mutuwar zaune harda dafe baki Da mamaki ainun HAJIA ta ce" Ahaf, Allah dai ya sa ba irin yan iska ka auro ba Magidanci!" Mahaifin Yumnah da mamakinta ya ce" Kennan du irin nasihar da na maki bata shiga kunnenki ba? Du irin rarashi da ban baki da nuna maki cewar hakan ba laifi bane tunda ba haramun aka aikata ba baki ji ba? Na nuna maki cewa ki guji janyowa yarki wulakancin namiji wani auren yake karawar ya kuma zane matar gidan a zauna babu abinda za'a yi baki yarda ba Kennan? Nan na fada maki in me kike takama da shi ke da y'arki ku ringa jin tsoron Allah a mu'amalarku ta yau da kullum baki fahimta ba Kennan?, In me kike takama da shi Akoy wace ta dama ki ta shanye, ke dinma da kike wannan ikirarin an fada maki tsoronki ya hannani karra aure? Bani da halin hakan ke kin san dalili da inada hakan da na karra , shine kike jinginuwa da wannan kina neman yiwa kanki mugun abu? Saki ko? Ba laifi, in sakin take so ya saketa ta tashi mu je, kema ki kwashi naki kayan ki barta a nan tunda nine ubanta ki tafi kema gida ki koyo hankali, Ni zaki mayar mutumen banza? Ni zaki wulakanta dan ina rarashinki? Bari ki ji in har Elhaji nada wata wace yake son karawa na rantse maki da Allah sai na yi gaya na tara jama'a kin dora abincin taron karin aurensa, da ke kika haife shi ai ba zaki ce haka ba, kuma da ke kika haifi KHausar din ba zaki ce a zaba ko ita ko matar gidan ba!, Ki kula in bakinki ya kuma budewa kika furtan shashanci a nan zaki gane shayi ruwa ne!" Shi yake fada HAJIA na sakin murmushi harda mikewa, su Baba kuwa hakuri suke bashi harda Akilah, su HAJIA nawarah kuwa kawunnansu nema suke su fi karfin gangar jikinsu dan kunya da tsoron wannan lamari Yana huci ya maida dubansa kan TAUFEEK ya ce" mun fi karfin mu zauna muna tambayarku daya bayan daya zata zauna ko a'a, gakanan gata in ta ce ka saketa na rokeka ka saketan ta zo gidan ta sameni ina jiranta, kuma ina neman alfarma Elhaji dan girman Allah yarinyar da aka aura masa ta tare gobe ko jibi, tunda ai ba wata bazawara bace bale ta kama zama a gidansu, dan Allah ka taimaka ta tare , itama mutun ce idan ya so in ta zo Yumnah ki hadiye zuciya ji mutu!" Daga nan ya mike yana kade babbar rigarsa ya umarci Akilah da HAJIA su mike su tafi Du yadda baba ya so dakatar da shi kiyawa ya yi a haka suka tafi suka barsu sai su ya su Ajiyar zuciya Baba ya sauke yana kallon Yumnah dake duke yanzu a tausashe ya ce" Tashi daga duken nan y'ata ki je kusa da Mamanku tashi kin ji?" Yumnah ta mike daga duken, maimakun ta je kusa da Mama sai ta je kusa da HAJIA ta zauna jikinta har rawa yake yi Baba ya sauke numfashi ya ce" Allah ya sanyaya, a yi hakuri dai, in sha Allah ko menene ALKHAIRI ne, ku ku tashi ku je bangaren ku tunda an gama, Allah ya sawaka" Jiki ba karfi su HAJIA suka tafi, aka bar su Mama da HAJIA baba, da Taufeek da baba da Yumnah Baba ya mike shima yana fadin" Sai da safe bari in je inada aiyuka a gabana, ka sameni da sasafe in sha Allah in baka takardun gidajen nan" "Kai d'an nan maganar tarewar fa?" HAJIA ta fada tana kallon Baba, Baba ya dakata ya dan juyo yana rage tsayinsa kadan ya ce" eh in sha Allah zan yi kiran Malam din abinda yace sai a yi" Mama kanta wasai take jin ranta, baba na ficewa ta mike tana gyara lafayarta ta dan rage tsayinta ta ce" Sai da safe HAJIA " HAJIA ta ce" Allah ya tashemu lafiya, ki yi addu'a dai kafin ki KWONTA kuma ki rufe dakin da ky, wannan kiyayar fa ta fara bani tsoro kar a bi dare a kasheki in shiga uku, baiwar Allah dubeta Magidanci solo solo da ita tsaf fa ake iya zane maka uwa dan da wahala in tana da karfi" Mama kam tafiyarta ta yi tana murmushi TAUFEEK ya juyo ya zubawa HAJIA ido bayan Yumnah ta mike ta haye da gudu gudu tana sakin kuka hajiar ta wani bankare ta ce" Ji abu ana guduma basa juyawa, wai Magidanci haka kake shaƙar bakin ciki?" A kausashe ya ce" Ke dai ki ji tsoron Allah, kina waje maimakun ke baba in kika buda baki kika yi magana dan ki kashe wuta ne, a'a, kina buda baki dan ki asasata ne, tsufa kike yi kina masifa, ki tuba kar ki mutu a haka !, Kuma ki yarda ki bi Ni Saudiya ban san yaya zan jijigaki kafin na sake ki a zagaye ba, kuma da kike cewa zaki aura min mace hudu kika kuskura kika karan aure sai dai ki zauna da su , a tsaya ana min auren dole dan an ga bana cewa komai, to Mama kika haifa da mai kwanoni ba Ni ba, dilla tashi ki tafiyarki Ni in je in bata hakuri kin wani rikitata" HAJIA ta yi zuru tamkar ta summa tana kallonsa ya mike yana harhada mata kayan turarenta Wani haushi ya tukota ta ce" Kai dai munafiki ne, auren dole? Eh lalle munafiki ne kai, yanzu Magidanci Ni zaka Duba kace an maka auren dole? Khausarar nan in tana waje idannuwanka a kan murje bakin siririya yake, in ta mike ka wani yi KISKIRIM kana leke ko dan ina rufa maka asiri? Munafuki sai na karra maka auren , ana maka gata kana ki, kuma zan je in fadawa mai kwanoni cewar kace a zagaye zaka batar da Ni kuma ka min aure, Allah dai ya shiryeka , kuma in ka ba wancen abar hakuri sai na kaika kotu!"......ta karashe tana jan habar zani tana share yan kwallah ta fice cike da haushi, ita ba komai ya fi bakanta mata ba irin wai ya je ya ba wancen hakuri, du irin rashin da'ar da ta maka masu? Lalle Bai nufi dakin Yumnah ba sai da ya je nasa ya yi wanka ya kimtsa kansa ya gama dukkan abinda yake sabo a gareshi sannan ya nufi dakin sai baza kanshi yake yi Fitilar a kashe take, ama kuma har yanzu shashekar kuka take yi a saman gadonta a dukunkune A hankali ya hau gadon bayan ya dafa ya ji daidai inda take kafin ya shige bargon a hankali ya shiga kokarin dago fuskarta a tausashe ya ce" Kai ina , Ni fa Ni fa Daf nake da gamawa in fara *AZAL* IN SHA ALLAH 😌😌😌😌😌😌 [7/19, 3:17 PM] Maman Aslam: 💔💔💔💔❤‍🩹❤‍🩹💔💔💔💔 *DA CIWO A ZUCIYATA* 💔💔💔💔❤‍🩹❤‍🩹💔💔💔💔 _MALLAKIN_ *SAJIDA NIJAR* *FREE BOOK NE* 4️⃣8️⃣ *GARABASA, GARABASA, PROMOTION, PROMOTION DIN LITATAFAN MARUBUCIYAR A KAN FARASHI MAI SAUKI 1K, YAN NIJAR KUWA 1000 FRANCS CEFA* 1: Duk karyar kada 2: Yar mahaukaciya 3: Neman na kaina 4: Bani da zabi 5: Bak'a ce 6: Kutkale 7: Makauniya ce 8: Mage 9: Duk nisan jifa 10: Idan ka raina inda kake 11: Dutse 12: Alkalamin kadarata 13: Bani da zabi 14: Dakika Biyar 15:Wata kokowar 16: Aure yakin mata 17: Ni zan ladabi 18: Daga tafia daukar soja *Dukansu a kan farashi mai sauki, zaka saka dubu guda ne domin promotion ne nake yi, ka tuntubeni kan layina kamar haka +227 93 81 16 18, Sajida Nijar* Now *Da CIWO A ZUCIYATA* *Tallah, tallah, tallah* *SECRET DE LA FEMME DU MANGA* _Gidan Kamshi, Sirrin Manyan Mata, nesa tazo kusa,Amarya ,Uwar gida,Ango da mai gida Har ma da yan mata da samari shin kuna sane da cewa HAJIYA FUSAM ta shirya tsaf domin gwangwaje ku da turarakunta masu dankaran kamshi? Tare Kayan gyaram jiki na musamman ,wanda daga nesa kamshin ki kadai ya wadatar ya isar da sakon zuwanki waje,gidan ki kuwa sai ya zam abun kwatance wajen kamshi, kar na cika ku da surutu bara in fara zayyano su_ Farar Humura Bakar Humura Humura special, humura de bain Humura epicé Lait de nuit Parfums désodorisant Parfums rideau et dras Lait de nuit Alkam Kulakcam *Waɗannan kadan ne daga bangaren turaran ruwa* Gagab, sandal flex, Durot, durus, sandal fleur, tafarce, farce, sandal bangui, sandal, hypotonic sandal, al'ut, coktail creation VIP, Gajiji, Mankaji, turaran wutar labule da cafet, Aba malan, boulettes *Munada bangaren gyaran jiki kamar haka:* mai mai saka santsin jiki, mai mai kanshi, Kayan gyaran jiki mai saka fata ta yi santsi da laushi, kayan gyaran jiki mai saka fata ta yi fari, Sabulu mai saka fata ta yi haske, sabulu mai saka fata ta yi santsi, sabulu mai goge yanayin fata, mai wanda baya saka fari mai gyara fata Sayen na gari mai da kudi gida,sai an gwada akan san na kwarai💃💃 Hajiya Fusam na zaune a kasar Niger domin yin magana da ita kai tsaye tuntuɓi wannan number 97 82 44 94 *SECRET DE LA FEMME DU MANGA* Gidan Kamshi, Sirrin Manyan Mata💃💃💃💃💃 A tausashe TAUFEEK yana kallon yadda gurbin idannuwanta suka yi rado rado fuskarta kuwa har wani hucin zafi take fitarwa ya talabeta sosai a jikinsa ya ce" ya dace zuwa yanzu ki yi hakuri da rigimar nan haka Yumnah, ya dace ki yi hakuri ki dauka haka Allah ya hukunta, kin ga ba ke kadai bace, saka abu a rai kin kusa min asara, bayan wannan fushin nan naki babu abinda baya saka ki, ya dace ki yi hakuri ki yi hakuri an bata maki ama Nima ki min uzuri ki kuma roki ALKHAIRIN dake tare da KHAUSAR a zamantakewarmu" Yumnah ta lumshe idannuwanta wasu hawaye suka sake biyo wa saman kuncinta, a raunane ta ce" Ta yaya zan iya danar zuciyar tawa? Na rasa ta yaya, tun kafin ka aureni na san cewa ina cin alfarmarta ne, a yanzu da ka aureni ta zamo itama matarka na tabbata zan zamo ne tamkar bola a gidan mijina, ban taba jin kishin mutun da kin kasancewarsa a waje irinta ba, TAUFEEK bana so, bana so Taufeek" A hankali ya sakata a jikinsa, hannunsa mai dauke da yalwantacen gashin hannu ya saka a hankali ya tare bayan keyarta, da dayan hannun kuwa ya ringa shafa bayanta a hankali idannuwansa a lumshe Shashekar kukanta ne ya fara daidaituwa sakamakon jinta a jikin da take gannin darajarsa da girmansa fiye da kowani jiki duniya, kanshin jikin da duminsa na sakata barci koda bata yi niya ba, fafadan kirjin na saka tsigar jikinta tashi, a hankali kunnayenta suka ringaa jiyo mata dadadar iskar bakinsa mai dumi a kunnenta A hankali ya juye da ita a cikin bargon ya zamo tana kasansa shi kuwa a sama Idannuwanta da sukai shame shame da hawaye yake kallo, cen kasan zuciyarsa kuwa kokowa yake yi da tarin tunanin wace take kila wa kalar rayuwarsa, wace bata kallonsa a matsayin katon dake iya kai keyarta kas, A hankali ya dan matsewa junnansu waje sosai , yana sinsinar wuyanta a tausashe cike da rarashi ya ce" Idan kika ga mace ta zama banza a gidanta, ita ta fara banzatar da kanta, ko a soyayata da ke ke ba banza bace da ban aureki ba, Yumnah, KHausar ta shigo rayuwarmu, Please kar ki ja, Bana so ki ja, bcz ni da kaina ban kwatanta ja ba, ki yi hakuri zan kasance mai KAMANTA adalci a tsakaninku ko dan gobena, I'm sorry wife " Kwarai ake cewa, dadadan zance na sanyaya zuciya haka ne, Yumnah na tare da tashin hankali da bakin cikin auren mijinta, sai dai irin yadda ya bata kulawa ya matukar saka ta ji yar Salama a zuciyyarta, ama tana kan bakanta, ba zata taba son KHausar ba, KHausar makiyaya take a duniyarta, kuma in sha Allah sai ta ci galaba a kanta, ba an aurawa mijinta ita ba, ta yi alkawarin sakata barin gidan nan da kaffafuwanta, in ta san wata bata san wata ba, ko ba komai ta rigayeta tashi tunda har ta rigayeta Sannin waye TAUFEEK a badini! Da kyar ta samu barci, shi kuma ya mike ya koma dakinsa yana jin yannayinsa du a takure A kan salaya ya kusan raba dare , yana fadawa Allah dukan damuwarsa Sai da ya gama sannan ya KWONTA da layin KHausar a hannunsa Yana so ya saka layin a wayarsa wani abu na hannashi, bai san me yasa yake so du wani abinda ya shige nata ya zamo nasa ne! Shi fa baya tunanin zai iya kawar da kai da wasu abubuwan, ama zai bi a hankali yadda komai zai zamo masa yadda yake so Washe gari kusan karfe goma ya sauko Yumnah ya samu a falo tana zaune da wayarta a hannunta Amsa wayar take yi, gannin ya sauko ta yi salama da wace suke wayar ta ajiye a gefenta tana kallonsa tamkar ta daukeshi da idannuwanta dan ya mata kyau sosai Zama ya yi gefenta kadan yana amsa gaisuwarta Sai da ya dan nutsu ya fuskanceta, da yannayi na serious bayan ya ji jikinta da sauki ya ce" Yumnah, ina so na sake maki magana a kan kula da mutunta Mama da HAJIA, ban kamaki da wani laifin da zan tuhumeki ba, ama ina dan tsintar wasu yannayi naki da basa min a wajen mahaifiyata, ki kula, nan din ba wajen da za'a kawo wargi bane, ki mutuntata su Yumnah ko dan haihuwata da suka yi!" Kai ta sada, muryarta a rarabe ta ce" Ka yi hakuri, ba abinda kake tunani bane, raina ne a bace" Bai sake cewa komai ba sai mikewa da ya yi ya haura sama Ajiyar zuciya ta sauke ta sake dauko wayarta ta dannawa mahaifiyarta kira, magana suke yi tunda safe kan maganar tarewar nan, lalle mahaifiyarta ta kwontar mata da hankali kan maganar, yanzu haka zata koma dakinta ne ta yi jiran sakon da za'a kawo mata, ta san cewa kamar yadda Mamanta ta fada maza basa son mace ruftata a bari ta taren sune zasu fitar da ita da nasu baiwar da Allah ya masu, ta kuma sake sanyaya mata zuciya cewar ta dakata ta gani ita dake dauke da cikinsa ta san ta gama shiga gaban du wata banza, danma babansu ya hannata fitowa da da kanta zata zo ta kawo mata dukkan abinda ta fada din A bangaren HAJIA kuwa tunda safe ta fice a gidan ta tafi kasuwa da direba, sai kusan karfe daya na rana ta dawo a lokacin manyan motocin kampanin furniture sun karaso har biyu shake da kayan daki na kasa da kasa sunna ciki sunna nasu aikin ta wuce bangaren su Mama ta je ta zube kayan da sisiyo ta saka Mama a gaba du irin kunyar da take ji ta sakata karanta mata abubuwan ita kuma tana warewa daki daki kaya irin na gyaran mata masu inganci har suka gama ta kwashi abinta da nufin zuwa ta fara dafawa ta saka a frij , maman kuwa ta yi murmushi tana girgiza kai cike da kunyar lamarin nan na HAJIA , sai dai ba halin nunawa ta shirya ta yi ficewarta itama dan zata je ne ta daidaita harkar kunshin Khausar din da kitso da dilkar da za'a yi mata a gidan HAJIA FUSAM GIDAN KANSHI Da gaske dai tarewar Khausar ta tabata dan Aba ya bada amanar ta tare din tunda har mijinta ya bukaci haka kamar yadda baba ya nuna Wunin ranar Yumnah bata kuma fitowa ba, abinci kuwa dama rabonta da shi tun anaa gobe auren aminiyar mijinta, idan ta ji yinwa takan samawa kanta ne bata bi ta cikinsa, dan ta kula idan ta bashi ko a'a ba zai zauna da yinwa ba tunda kakarsa na gefe A bangaren TAUFEEK kuwa sai dare ya dawo gidan, yauma shi dai ya samu Yumnah a bangarenta, gwargwadon iyawarsa ya kwatanta bata kulawa , ko dan abinda ke cikinta, sannan har ga Allah yana so ya bata darajar ta daidai misali, dan baya so ya shiga hakinta ko kadan, Khausar kuwa dama yau bai ganta a wajen aiki ba, bai kuma je gidan ba, dan ya dan tsinci cewar tana cen tana kuka, bashi da amsar bawa kansa sai girgiza kai da ya yi ya ci gaba da lamuransa, abu daya ne ya sani rikici ne Mai kwanoni da Malan muntari sun daurawa kansu, mai kuncewa fitar ransa ne daga gangar jikinsa, gwarama Yumnah da Khausar su ba kansu lafiya ko su yi, zai kasance mai raka du wani mai doguwar tafiya ne har su kai inda yake so bi'izinilah A gidan su KHausar Hajia Fusam ce da kanta ta yiwa gidan dira tun a lokacin da Mama ta je mata da bukatarta suka yi magana irin ta manya suka kuma shirya cikin harka ta manya, da kanta ta dauki motarta bayan Maman ta mata kwatance ta kuma sanarwa Maman su KHausar din cewa za'a zo a shiga kimtsa Khausar din Kaya ne ta je da su na kasa da kasa, ko da ta karasa su Rukaya ne suka tayata saka kayan cikin gidan Aba dan da yawansu Du irin yadda Khausar ta rikice da bayanin wai kwana biyu kawai zata je gidan su TAUFEEK matsayin mata a wajen TAUFEEK sai da Mama ta mata magana daya da ta sakata sakarwa ta zubawa sarautar Allah ido Hajia Fusam ta fara ne da hada hadin da zai goge kunshin da aka yiwa Khausar ta shafa mata aka bari na dan lokaci kankani aka wanke da ruwan dumi, sai kuma ta kawo hadin da ta yi dan dora Khausar din a kujera hadi na mamaki ta saka Khausar din mikewa ta shafeta da shi ama fir ta ki yarda har wasu sassan jikinta sai ita da kanta ta shafa irin su Mamanta da cinyoyinta da mazaunanta, ita dai Fusam ta bata damarta dan ko ba komai budurwa take mai kunya abinda dai ya tabatar shine ko'ina ya samu sannan ta haudata kujerar nan ta rufeta da rigar da ake rufewa aka bar fuskarta kadai a waje Hayaki na ratsata har cije lebe take yi dan sosai yake ratsata, gefe guda kuwa Hajia Fusam na aikin hade haden gyaran fuska da lebe da kuma na raba rabar cinyoyi da mazaunai, hadi dai na mamaki , ga kuma hadin madara mai sanyi da ta sakawa zuma ta mata da magani mai kyau da inganci namu jikake na wajen Maman khair tana yi tana kafa mata tana sha har suka gama aka sauka aka nufi bayi dan wanke kwanin Tana fitowa Fusam ta kama dirzarta da dilka, tamkar zata kwaye mata fata dan kuwa bata yi mata da sauki ba , sosai ta darjeta har tana yan hawaye , shima aka darwaye da ruwan dumi aka kuma hauda mata kurkum hadi mai madara sannan ta dawo fuskarta ta shafa mata hadin tumatur,....a wannan rana dai Khausar ta ga ikon Allah dan hadi kan hadi ake juye mata ga na sha a gefe sai da ta ji cikinta tamkar zai fashe, ga lebenta da aka samu da nasa hadin aka darje shi da bruch har sai da ya ringa wani irin MUSMUS a ido bale a tabawa , kafin ta kare da sakata a babar robar Mama ta wanki cikin rantsatsen turaren mata masu daraja, su turarukan nan kala uku ne, dama aikinsu ratsa jikin mace ne dan ba'a shiga da pant sai da ta shiga ya zauna ta rufa jikinta da zani sai dan zabura take yi saboda zafin ruwan da aka zuba turaran ciki Tana zaune a cikin ruwan Fusam ta ajiye kujerar tsuguno a bayanta ta shiga gyara mata gashin kanta ta hanya shafa mata hadin lallen da ta hada shi da sinadaren gyaran gashi da kuma turaren gashi mai nutsatsen kanshi bayan ta rereda shi ta ringa fesa hadin danyar cita da kananfari da ta markada ta matse ruwa ruwan ta zuba a abin fesawa ta fefesa mata shi sosai sannan ta saka mata hular kan ta daure mata shi tam Sai kusan magariba suka gama shirin yau, tana tsaye a kanta har ta dauro alwallah bayan ta kuma yin wanka da wani hadin ta zo ta tayata shafa man da ta hada mata mai karra laushi da santsin fata ta sakata a gaba ta ci dahuwar kazar amarya mai ridi da nonon rakumi ta kuma bata tsumi matsayin ruwa sannan ta zauna har suka yi sallar isha ta masu salama bayan ta tabatar mata gobe idan Allah ya kaimu zata dawo tun da duku duku duku mai kunshi da mai kitso , sannan ta tafi Bayan tafiyarta sosai Khausar ta so tsundumuwa a tunani, sai dai wani irin kanshi da laushin shinfidar da aka yi mata ya luliyata a barci mai nauyin gaske, ko ba komai wannan dirza da ta sha da gasuwa da ruwan dumi sun isa su sakata barci koda bata yi niya ba Mama kam ta kwana saman salaya Tana neman alkhairin auren nan da kuma adu'ar Allah ya kade dukkan wata fitinar dake iya kunnowa, ya kawota da sauki, fatanta yarinyarta ta amshi aurenta ta kuma je ta yi biyayya a dakin mijinta, sun yi magana sosai a kan tarewar, Aba ya nuna damuwarsa na yana so ya yi mata kayan daki ama Baba mai kwanoni ya daureshi da jijiyoyin jikinsa ya hannashi maganar kayan dakin, duda haka tanadin da ya yi dan kayan dakin da garar sai ya zuba kaf a Gara , ya yi niya zai mata Gara ta mamaki, mamama ta yarda da haka, babu abinda ya gigitasu harda makota irin akwatunan da aka kawo, ta san aure wani lamari ne na Ubangiji, lalle Khausar ta yi goshi na mamaki, maganar akwatunnan Khausar har gidan su tsohon saurayinta ya kai, wace ta kai maganar kuma ita ta kawowa mama cewar mamansa na cewa auren jari aka yi, Maman kuwa ta bata amsar ai ba laifi bane, ba haramun bane ! Babar rana Rana bata karya sai dai uwar diya ta ji kunya in ji yan magana A dade ana yi kuma sai gaskiya A yau ranar asabar ta kama babar ranar da ta zamto ranar tarewar Khausar a dakin mijinta, amini a gareta, abokinta bisa hukuncin ubangiji ba tare da shirinta ko yardar ta ba sai dan hakan shine a rubuce a kundun tarihinta, tsayin shekaru tana rayuwarta tare da kalolin tsangwamar mutane da tsangwamarta ta kanta, a yanzu ta amsa kiran matar AURE, auren da take yiwa kallon wasan yara, wanda ta gama yarda har a zuciyarta cewa ta girmami wannan aure nema ake yi a hadata da shi dan ta shiga uku, sai dai ta makara, domin sauko ta yi ba tare da ta san shi a hanya ya kwana ba, a daidai wannan lokacin da magariba ta sanyo kai ya zamto a dole Mama ta cire kunyar y'ar fari ita da yar uwarta suka tsaya a dokin kofar dakin Aba suka hanna mutane shigowa Wato wani irin taro ne na mamaki ya dauka har anguwar ba iya gidan Aban ba Mama bata yi gaya ba, hakama Khausar, dama dama su Aisha sun gayyaci daidaikun kawayensu , sai ga abin mamaki matan anguwa tun kafin magariba ta rufa suke shigowa kowace kuma da haramar rakiyar amarya Khausar, domin da yawa daurin auren a wai suke jinsa, an daura din wasu basu san waye angon ba, irin yadda ta yi rayuwarta kuwa zasu so su ga wanene wannan ango! [7/19, 3:17 PM] Maman Aslam: 💔💔💔💔❤‍🩹❤‍🩹💔💔💔💔 *DA CIWO A ZUCIYATA* 💔💔💔💔❤‍🩹❤‍🩹💔💔💔💔 _MALLAKIN_ *SAJIDA NIJAR* *FREE BOOK NE* 4️⃣9️⃣ *GARABASA, GARABASA, PROMOTION, PROMOTION DIN LITATAFAN MARUBUCIYAR A KAN FARASHI MAI SAUKI 1K, YAN NIJAR KUWA 1000 FRANCS CEFA* 1: Duk karyar kada 2: Yar mahaukaciya 3: Neman na kaina 4: Bani da zabi 5: Bak'a ce 6: Kutkale 7: Makauniya ce 8: Mage 9: Duk nisan jifa 10: Idan ka raina inda kake 11: Dutse 12: Alkalamin kadarata 13: Bani da zabi 14: Dakika Biyar 15:Wata kokowar 16: Aure yakin mata 17: Ni zan ladabi 18: Daga tafia daukar soja *Dukansu a kan farashi mai sauki, zaka saka dubu guda ne domin promotion ne nake yi, ka tuntubeni kan layina kamar haka +227 93 81 16 18, Sajida Nijar* Now *Da CIWO A ZUCIYATA* *Tallah, tallah, tallah* *SECRET DE LA FEMME DU MANGA* _Gidan Kamshi, Sirrin Manyan Mata, nesa tazo kusa,Amarya ,Uwar gida,Ango da mai gida Har ma da yan mata da samari shin kuna sane da cewa HAJIYA FUSAM ta shirya tsaf domin gwangwaje ku da turarakunta masu dankaran kamshi? Tare Kayan gyaram jiki na musamman ,wanda daga nesa kamshin ki kadai ya wadatar ya isar da sakon zuwanki waje,gidan ki kuwa sai ya zam abun kwatance wajen kamshi, kar na cika ku da surutu bara in fara zayyano su_ Farar Humura Bakar Humura Humura special, humura de bain Humura epicé Lait de nuit Parfums désodorisant Parfums rideau et dras Lait de nuit Alkam Kulakcam *Waɗannan kadan ne daga bangaren turaran ruwa* Gagab, sandal flex, Durot, durus, sandal fleur, tafarce, farce, sandal bangui, sandal, hypotonic sandal, al'ut, coktail creation VIP, Gajiji, Mankaji, turaran wutar labule da cafet, Aba malan, boulettes *Munada bangaren gyaran jiki kamar haka:* mai mai saka santsin jiki, mai mai kanshi, Kayan gyaran jiki mai saka fata ta yi santsi da laushi, kayan gyaran jiki mai saka fata ta yi fari, Sabulu mai saka fata ta yi haske, sabulu mai saka fata ta yi santsi, sabulu mai goge yanayin fata, mai wanda baya saka fari mai gyara fata Sayen na gari mai da kudi gida,sai an gwada akan san na kwarai💃💃 Hajiya Fusam na zaune a kasar Niger domin yin magana da ita kai tsaye tuntuɓi wannan number 97 82 44 94 *SECRET DE LA FEMME DU MANGA* Gidan Kamshi, Sirrin Manyan Mata💃💃💃💃💃 Nasiha Aba ke yi mata, yana zaune ne saman kujera Khausar na zaune bakin katifar Aban Du yadda Aba ya so kar ta yi kuka , shima kar ya yin sai gashi shine ya fara sada kansa yana mai fashewa da kukan da ba sauti Ya Allah, Allah mai iko Allah mai amsa adu'ar bawansa Ashe zai ga wannan rana? Ashe zai ga auren Khausar dinsa? Auren da yake kyautatawa zaton ba hadi ne suka yi daga sama dan jin dadinsu ba? "Ya Allah alfarmar fiyayen halitta ka zaunar da y'ata a dakinta, ka kade duk wata fitina ka sa ta zamto mai biyayya wa mijinta" Aba ya fada bayan ya dago kansa yana kallonta A rikice ta idasa fashewa da kukan itama ta sauko tana rarafowa har daf da kafar Aban ta dora kanta a hannunsa, kan da ya sha kitso , hannun da ya sha lalle , idannuwanta kawai aka sakawa kwali sai dan jan baki mai ruwan kasa dan a boye hasken jan lebenta wa kowani mutun ya zamto na mijinta ne shi shi kadai, a birkice ainun tana fitar da dadadan sanyayan kanshin lafayar dake jikinta da kuma kanshin fatar jikinta ta daban ta ce" Aba, Aba ba zan iya ba, Aba Ni babu inda zan je" A tausashe sosai Abanta ya rike fuskarta yana murmushi ya ce" Dan ina kuka?" Khausar ta gyada kai ta ce" dan kana kuka Abana na fasa auren !" Abanta ya saki yar dariyar da bai shiryawa ba, a hankali ya ce" Kukan farin ciki nake yi, kukan jin dadi nake yi, kukan godiyar Allah nake yi, kin ga ai mun gama maganar rikicin kin fasa auren ko? Ai zaki je ki zauna mu gani ko?, Y'ar Aba, ki kasance mai biyayya, kar ki saki ki yadda tarbiyyar ki komai rintsi, ki sani ba wayonki ko dabarar ki ko rashin kunyar ki zata saka a so ki ba, ki kasance mai biyayya mai gaskiya mai addini da tsoron Allah, wannan shine zai ja gabanki har zuwa aljannah, kin ga tun dazu ina jin hayaniyar cewar motoci sun karaso , nima zan zo gidan ai kin ga ina zuwa wajen hajia ko? Zan zo gobe goben nan in sha Allah, kuma kin ga aikinki zaki ci gaba da tafiya ko? Share hawayen nan kar na gani kin ji?" Khausar na sauke ajiyar zuciya mahaifinta na sake rarashinta a cen kofa kuwa motoci ne na mamaki suka zo daukan amarya wanda tun a nan kallo ya koma sama, shawo ya dau Giwa Ba wasu motoci Masu yawa bane dan ba zasu wuce goma ba, ama a cikinsu aminai ne na kusa da kusan PROFESSEUR, a yau ya sauka a kasar dan zuwa daukan bestyn besty, wato kawar amini ce kuma aminiyar amini, shi kuma a yau yake da maganar hayata irin wace ya tanadar masu A hankali ya yi murmushi ya kuma kashe kiran da ya shigo wayarsa na Professeur A kalla kiran nan ya kai na hudu da yake masa idan ya daga sai ya yi shiru ya ki fadin komai Lalle shi yake da godiyar yiwa baba da ya kasance uba jajirtacen da bai bar professeur summa a kan bege ba Dan buga masa madubin da aka yi ana miko masa waya ya saka shi sake sakin murmushi a hankali ya karra a kunnansa yana janyo doguwar salama A zuciyarsa ya amsa salamar ne? Ko baima amsa ba? Allah masani, abinda ya fada shine" Yaya na ga har tara zata yi shiru?" Dariya Alhusain ya yi kasa kasa ya ce" Inspector an hanna mana Besty fa, wai sai gobe" Shiru ya yi, irin shirun nan na daukewa gaba daya tamkar wanda ya ajiye wayar, a hankali ya furta" Baka iya ware abin wasa da wanda ba na wasa ba?" Wannan karron Alhusain ya bushe da dariyar da ta saka TAUFEEK katse wayarsa ya sake yin kicin kicin ya zubawa Hajia ido wace ta ci uban bando sai kai kawo take yi ta tara tsofafin irinta a falo har wannan lokacin basu tafi ba wai amsar amarya zasu yi Sai da suka yi ido hudu Hajia ta saki murmushi ta wani gyara tsayuwa ta ce" Kai wai wani kinibibin kake min a daka ne ? Ko auren dolen zaka kunce? Kawai ka kara gaba malan ka sa sai shigowa nake da salama Ni da dakina!, In dai Khausara ce a nan zata tare tunda auren dole na maka sai mai kwanoni ya san abin yi , aikin banza!" Sshi dai bai tankata ba, har ta gama ta fice tana yade yaden habaici ta koma bangaren Mama, wace ke zaune a baban falon yau itama, itace zaune darr sai bakinta dake zaune tare da ita kowane cikin shiga ta alfarma an dafa abinci na alfarma an ci yanzun jiran saukar amarya ake yi dan a amsheta sai kowa ya kama gabansa, sai dai a taron nan kaf babu matan mai kwanoni da Yumnah, domin ita Yumnah tana cen dakinta ta rufe tana nata shagalin, vidio call da kawarta bayan ta gama waya da mahaifiyarta, du cikin kwontar mata da hankali suke yi, burinsu ta kwontar da hankalinta ta kuma fara aiwatar da abinda suka shirya tun a yau, dan babu abinda zai sa su yarda TAUFEEK da Khausar su zama abu daya! Sai kusan tara da rabi motocin daukan amarya suka karaso Mutunci irin na Hajia FUSAM tare take da kanwarta a rakiyar amarya , tana rike da wani mahaukacin turaren alfarma cikinsa fulawowi ne bayan nada nata lafayar da ta yi saman wando irin mai likewa a jikin nan da riga mai dogon hannu sai ta rufa mata alkyaba fara kall , ya zamto kanwar Mama rike da Khausar, su Rukaya sunna rike da wasu yan abubuwanta, Hajia Fusam na fesa turare a dukan tafiyarta, abin sai wanda ya gani daukaka Allah ya daukaka y'ar gidan Aba A hannun Hajia aka damka KHAUSAR, bayan an dukar da ita ta gaishe da Hajiar A nutse Hajiar ta bude alkyabar Khausar tana murmushi ta ce" Masha ALLAH khausara masha ALLAH" A hankali Khausar ta fashe da kukan da take rikewa lebe har yana yi mata rawa a hankali ta dora kanta a cinyar Hajia wace ta kwashi salalami tana kallonta ta ce" Ke dan kaniya nan din ba gida bane? Ni kar ki sakani kuka bayan na dinka ba takashin kowa ba na buga daurin bando na rangada kwali abina kin ji ko?" Mama ta saki murmushi, a hankali ta karaso daf da Hajiar ta zauna, a nutse ta saka hannunta ta dago Khausar ta saka tissu tana share hawayenta , da kula ainun ta ce" Ya isa haka mana, na san kukan ne kike ta yi tun safe ko? Tashi ku je ki huta, Allah ya maku albarka ya yiwa rayuwar aurenku albarka" "Kai na Annabi yace amen!" Hajia ta fada tana kallon jama'ar dake daukan vidio ne, hoto ne, da masu amsa adu'ar, kai abu dai masha ALLAH, haka Hajia ta ja Khausar sauran na biye da ita suka karasa bangaren TAUFEEK kasa kasa tana fada mata magana kamar haka" ke yi shiru abinki, abinda an daina yayin kuka? Kuma yau din da na kawo ki nan dan gudun yan uba ne, gobe cen bangaren nawa zaki kaura fa kin ji ? Share hawayen kar ciwon kai ya hannaki rawar gaban hantsi!" Da haka har suka karasa suka shigar da ita da addu'a aka haura da ita rantsatsen dakinta dake daf da na Yumnah aka zaunar da ita a gefen gadonta Sosai danginta da yan rakiya suka yaba mutunci da karamcin ahalin mai kwanoni sannan suka tafi da addu'ar alkhairi suka bar Khausar na sauke ajiyar zuciya tana jin abin wani iri tamkar a mafarki Ta dauki lokaci a zaunen nan har ta kage, A hankali ta mike ta sauke alkyabar da aka naɗa mata ta nufi wajen madubin dakin mai girma wanda gabansa ke cike da tarin turaruka na alfarma kala kala ta ja ta tsaya tana kallon abin hannunta da su zoben da aka saka mata A nutse ta sabule alkyabar gaba daya ta ninke ta ja kujerar ta ajiye sannan ta zubawa fuskarta ido har zuwa tsarin halitar da Allah ya yi mata Da kunya ta kauda dubanta, dan a kulun takan ji kunyar kirarta sosai, bata son tsarewa kanta ido dan abin na bata kunya, bale yau da aka yi mata kwaliya irin ta mata masu aji sai ta zama tamkar ba ita ba Wandon ne na ciki baki mai santsin nan da kama jiki wanda ke rike cinyoyi taf, sai farar rigar mai dogon hannu itama a jikin take, sai bakin dan kwalin da aka yiwa dauri irin na zara Buhari daurin da ya hau kan kitsonta das ya kawata fuskarta da dan wajen gefe da gefen nan na mata mai kyau ya yi mata luf masha ALLAH, du kuwa irin kukan da ta sha hakan sai bai boye tsararan kyan da ta zuba ba a yau Idannuwanta ta rintse sakamakon jin karar bude kofar dakin gabanta na dokawa, dan ko wanene a yanzu ya shigo bata raba dayan biyu ko matar gidan ko mijin matar gidan ne Ta madubi ta dan bude idannuwanta jin ba'a yi mata salama ba, kuma kamar an shigo ta zuba dubanta a kan fuskarsa Da sauri ta dauke duban nata, hannayenta suka dan fara rawa Gaba daya yau tamkar an karra masa cika ido da girma a idannuwanta Shigarsa ta ɗinkin shada ne ruwan maroon , kansa dauke da hula A tsayen da yake jinginuwa ne ya yi da garun dakin ya zuba mata ido da irin kallon nan da ba kyau ana yinsa wa mutun fa ai ko? A hankali ya sauke ajiyar zuciya ya ringa takowa har inda take tsayen nan tana ta kiciniyar kunce agogon da aka daura mata ta gaza ya tsaya daf da bayanta bayan ya zubawa bayan nata ido a hankali ya sauke dubansa a wajen kugunta daidai inda ya lotsa saboda tudun mazaunanta da fadinsu sai ya zamto nan daidai tsatsonta kamar tana masa da gangan ko dan ta nuna kirarta bayan haka Allah ya haliceta kwatuwar wajen ne ya sa nan din karyewa da fitar da shap dinta sosai A hankali ya sako hannayensa ta bayan nata ya dora hannayen nasa saman nata ya rike agogon yana kunce mata a nutse hakan ya sa ta dago a tsorace ta zarro idannuwa tana kallonsa ta madubin Shima dagowar ya yi ya saka nasa idannuwan a cikin nata Wa'inda a yau ya kasa boye dukkan nau'in abinda ke zuciyarsa a cikinsu, suka bayyanar da shi suka tona shi A cikin makoshi ya budi bakinsa kadan ya ce" Barka da zuwa gidanki *MY WIFE*" A rikice ta sake zuba masa ido, sai kuma ta buda hannayensa ta juyo da sauri dan son fita daga wannan mugun tashin hankalin da yake son sakata gabanta na dokawa, sai dai tana juyowar ya zamto yanzu ido cikin idon ba ta madubi bane suke yi, ta gar da gar ce Da sauri ta sada kanta, lebenta sai son kiran sunnansa yake yi ama ta gaza fitar da amon Ajiyar zuciya ya sauke a hankali ya dan matsa baya kadan sannan ya kamo hannunta kasa kasan ya ce" Zo mu je" Kasa hanna kanta binsa ta yi, du kuwa da irin yadda jikinta ya mata nauyi har suka karasa kofar dakin Yumnah ya dakata ita a gefensa kadan yana kallonta ya dan buga kofar ta sake zuba mata ido Basu wani dauki lokaci ba suka ringa jin nishinta da kyar Da sauri Khausar ta dago kanta daidai lokacin da Yumnar ta bude kofar da kyar , sai luuuuuu ta fado jikinsa tana sakin hannayenta gaba daya tamkar wace ta tafi duniyar summa Ba wai shi ba da bai shiryawa haka ba, ita kanta Khausar sai da ta kwala ihu a tsorace tamkar ba likita ba tana ja baya kadan sannan ta yiwo gaba tana kama masa da taya shi ambaton sunnan Yumnar A rikice ta mike tsaye tana fadin" Ina valise dinka? (Wato ta likitocin nan ta duba marar lafiya)" Rudewarsa bata kai Tata ba sam, shi dai ya talabi Yumnah ne yana kiran sunnanta da dan buga gefen kuncinta A nutse ya mike da ita tsaye ya juya yana sauka Khausar na biye da shi ya ce" Tana part din Hajia" Bata tsaya jiransa ba ta wuce da gudu, abinka da likita kamar masu wani boyeyen tsumi idan suka hadu da marar lafiya a waje, ta je bangaren Hajia wace ke sauraron wa'azin karfe goma ta fada da gudu gudu bayan ta yi salama ta ce" Hajia, ina akwatin TAUFEEK ta asibiti?" Hajia kiris ya rage bata fado ta kai ba ta mike jiki na bari ta ce" Me ya samu magidancin? Innalilahi na shiga uku, gatacen a kasan gadona " Kafin Khausar ta fito ta sanar mata Yumnah ce ba lafiya tuni ta nufi bangaren TAUFEEK din sai salalami take yi hawaye kuwa tuni ya bale mata Khausar ta dauko da saurinta tana jin abin nan kiris ya rage ya tadeta dan sai da ta rike abu da ya dabaibayeta ta rasa yaya zata yi sai kawai ta karasa kofar falon da kyar ta tsaya ta warware nadin kaf dinsa ta yarfa a gefen kafada ba tare da tunanin komai ba ta shigo da akwatin da dan sauri ta kawo daf da shi sannan ta zauna ta bude tana kallonsa ta ce" Me zan miko?" Sai a lokacin Hajia da ta turo baki ta juyo ta kalleta da niyar kai nata rankwashi ta kuma sileta tasss dan ta kusa hadasa mata hawan jini ashe wannan ce take marmarmartu kamar ta summa bayan ita sai ta rantse da huwan rahamanu karya ne dan ta hanna magidanci rawar gaban hantsi ne, ita kuma ta wani je a guje kamar mai kwanoni ne ba lafiya mai malan muntari tsabar rashin Sannin ciwon kai sai kuma ta yi arba da Khausar din a Khausar dinta Ido ta fara fitarwa, sai kuma ta tafa hannunta ta ce" lah lah jama'a astagfrullah ke y'ar nan ke ce?" TAUFEEK dake kallon yannayin Yumnah yana tunanin to mema zai yiwa Yumnar domin ba jinnin ne ya dawo ba, yana daf da cewa Khausar ta bashi abin auna hawan jinni maganar Hajia ta saka shi dagowa shima ya kalli Khausar din, daidai ta rikice tana son warware lafayar da bata san ta inda zata maidata ta daura ba, kawai sai ta mike da gudu ta nufi haurawa sama tana mai fashewa da kukan takaici har ta bacewa ganninsu dan kuwa TAUFEEK da Hajia da suka daga kai suka bi mata da kallo sai da ta bacewa ganninsu sai kuma suka juyo a tare suka yi ido hudu shi da Itan TAUFEEK ya daka fuska yana hade girar sama da ta kasa ya ce" MEYE!?" HAJIA ta tabe baki ta dauko akwatin ta turo masa daf da shi da gunguni tana gyara daurin kalabinta ta ce" Hi PEOPLE 😍😍😍😍 Maganar adabi ce muke: A tafiyar labarin *AZAL* ina dauke da *ADABI* ne kamar haka Zamantakewa Yaki a soyaya Kauranci Bariki Ya rab ka nuna min ranar fara shi lafiya idan har alkhairi ne [7/21, 8:25 PM] +234 708 653 0343: 💔💔💔💔❤‍🩹❤‍🩹💔💔💔💔 *DA CIWO A ZUCIYATA* 💔💔💔💔❤‍🩹❤‍🩹💔💔💔💔 _MALLAKIN_ *SAJIDA NIJAR* *FREE BOOK NE* 5️⃣0️⃣ *GARABASA, GARABASA, PROMOTION, PROMOTION DIN LITATAFAN MARUBUCIYAR A KAN FARASHI MAI SAUKI 1K, YAN NIJAR KUWA 1000 FRANCS CEFA* 1: Duk karyar kada 2: Yar mahaukaciya 3: Neman na kaina 4: Bani da zabi 5: Bak'a ce 6: Kutkale 7: Makauniya ce 8: Mage 9: Duk nisan jifa 10: Idan ka raina inda kake 11: Dutse 12: Alkalamin kadarata 13: Bani da zabi 14: Dakika Biyar 15:Wata kokowar 16: Aure yakin mata 17: Ni zan ladabi 18: Daga tafia daukar soja *Dukansu a kan farashi mai sauki, zaka saka dubu guda ne domin promotion ne nake yi, ka tuntubeni kan layina kamar haka +227 93 81 16 18, Sajida Nijar* Now *Da CIWO A ZUCIYATA* *Tallah, tallah, tallah* *SECRET DE LA FEMME DU MANGA* _Gidan Kamshi, Sirrin Manyan Mata, nesa tazo kusa,Amarya ,Uwar gida,Ango da mai gida Har ma da yan mata da samari shin kuna sane da cewa HAJIYA FUSAM ta shirya tsaf domin gwangwaje ku da turarakunta masu dankaran kamshi? Tare Kayan gyaram jiki na musamman ,wanda daga nesa kamshin ki kadai ya wadatar ya isar da sakon zuwanki waje,gidan ki kuwa sai ya zam abun kwatance wajen kamshi, kar na cika ku da surutu bara in fara zayyano su_ Farar Humura Bakar Humura Humura special, humura de bain Humura epicé Lait de nuit Parfums désodorisant Parfums rideau et dras Lait de nuit Alkam Kulakcam *Waɗannan kadan ne daga bangaren turaran ruwa* Gagab, sandal flex, Durot, durus, sandal fleur, tafarce, farce, sandal bangui, sandal, hypotonic sandal, al'ut, coktail creation VIP, Gajiji, Mankaji, turaran wutar labule da cafet, Aba malan, boulettes *Munada bangaren gyaran jiki kamar haka:* mai mai saka santsin jiki, mai mai kanshi, Kayan gyaran jiki mai saka fata ta yi santsi da laushi, kayan gyaran jiki mai saka fata ta yi fari, Sabulu mai saka fata ta yi haske, sabulu mai saka fata ta yi santsi, sabulu mai goge yanayin fata, mai wanda baya saka fari mai gyara fata Sayen na gari mai da kudi gida,sai an gwada akan san na kwarai💃💃 Hajiya Fusam na zaune a kasar Niger domin yin magana da ita kai tsaye tuntuɓi wannan number 97 82 44 94 *SECRET DE LA FEMME DU MANGA* Gidan Kamshi, Sirrin Manyan Mata💃💃💃💃💃 Hajia ta tabe baki ta dauko akwatin aikin ta turo masa daf da shi tana guna guni ta ce" Miya ce, ai yau ka ga me nake nufi da ana gudu abu ba motsi, sai ka yarda a maka sakiyar da ba ruwa malan!" Shi dai bai kuma bi ta kan Hajiar ba, Yumnah dake kwonce jikinsa tamkar wace ba rai a jikinta ya zubawa ido , kallonta yake yi zufa zufa na tsatsafowa a gaban goshinsa A hankali ya sauke ajiyar zuciya a tausashe ya ce" Yumnah, ki buda idannuwanki" Sosai gabanta ya fadi jin maganarsa, kar dai ya gane lafiyarta kalau? Sosai kirjinta ya ringa dokawa da tsoron kar aje ya gane cewa lafiyarta kalau ne A nutse ya mike da ita ya haura saman dakinta da ita Ruwa ya haɗa a dan karamin bokici da farin tawul ya zauna daf da ita, a nutse ya ringa dan matsewa yana dan goge mata goshinta sannan ya kunna mata kira'a Bayan ya gama still yana zaune ne rike da hannunta dan ba zai iya tafia ya barta a wannan halin ba, duda babu abinda ya fito filin da a matsayinsa na likita ya gani na daga hankali, tana numfashinta normal, ama tunda ta yi haka sai ya bita a hankali ko dan abinda ke cikinta Tun tana summan gangan har barci ya fara fizgarta a hankali barcin ya dauketa ama a kala ta kai karfe biyu da wani abu na dare Mikewa ya yi bayan ya gyara mata kwonciyarta ya fice a dakin Wani irin abu yake ji mai kama da bacin rai a kasan zuciyarsa, ama ya dane ya karasa kofar dakin Khausar a hankali ya dan murda kofar Jin a rufe ya saka shi sauke ajiyar zuciya ya nufi nasa dakin Da kyar ya samu barci ya dauke shi, cike da bege da tarin kuncin abinda yake tunanin na nema ya fara zama rainin hankali A bangaren Khausar kuwa, tarin kunyarsa ya saka tana shigewarta ta saka sakata ta karaci kukanta sannan ta je bayi bayan ta gama karewa bayin kallo ta yi wanka ta fito ta bude bangaren tufafinta ta dauki riga marar nauyi ta saka ta fesa turare a jikinta sannan ta saka hula fara ta je ta yi addu'a ta kwonta tana ta shaƙar sansanyan kanshin sababin kaya da turaren dakin har barci ya dauketa cike da jin kewar iyayenta Tunda asubahi ta mike ta yi sallarta sannan ta shiga dan kai kawonta tana ta duba tufafinta da tunanin abin sakawa dan zuwa wajen aiki Karfe takwas saura ta gama shiryawa cikin shiga ta leshi da abaya mai shara shara ta dauki jaka yar madaidaiciya da takalmi mai hawa da abayar sannan ta fito ta rufe dakin nata ta dan dakata da tunanin ina zata ga Yumnah dan ta tambayeta jikinta? Domin a tunaninta idan har ta tafi ba tare da ta tambayeta jikinta ba, bata kyauta ba Dakin nata ta nufa hankali kwonce ta kwonkwasa sannan ta dakata tana jira a bata damar shiga A kalla ta kusa minti uku tana sake neman izini harda salama dan a tunaninta ko ba'a jita bane? Sai cen ta ji an bata damar shigowa ta hanyar fadin" Cm in!" Aka yi shiru Dan jim ta yi sai kuma ta tura tana sake yin salama idannuwanta a kan Yumnar dake zaune fess da ita cikin rigar barcin dake dan bayyanar da wasu sassa na jikinta kamar cinyoyinta da hannayenta Kanta ta kawar kadan tana nuna alamun zata juya ta ce" Barka da safia Yumnah, yaya saukin jikin? Dama wajen aiki zan je nace bari na ga jikinki" Bata da niyar tsayawa bayan tambayar da ta yiwa Yumnah dan yannayinta bai dace ta tsaya din ba, tunda shiga ce da iya mijinta ya dace ya gani a nata tunanin, dan haka tana maganar ne tana kokarin juyawa ta ji Yumnah cikin muryarta tamkar ba zata fadi mai zafi ba ta yi murmushi ta ce" Bani da lafiya ne dama?" Khausar ta dan dakata , a hankali ta juyo tana kallonta, sai kuma ta dauke dubanta ta ce" baki da lafiya mana, ba summa kika yi jiya da dare ba?" "A'a, lafiyana kalau" Yumnah ta fada tana sake sakin wani murmushi Sai kuma ta sake kallon KHausar ta ce" Mamaki nake yi, amarya da zuwa aiki washe garin tarewarta? To wai budurcin ne ba'a kawo ba ko kuwa jarumina ne ba zai iya kallon guzuma ba?" Sosai Khausar ta ji nauyin maganar nan, ko dan bata riga ta bi ta hanyar ba, ko kuwa har yanzu a wai take kallon abin? Maganar dai ta matukar bata kunya da mamaki daga bakin yarinya karama Kamar Yumnah Shin wai me ta yiwa Yumnah ne? A tunaninta koda wani zai kulaceta banda Yumnah, dan ta san wacece ita a taka rawar aurenta da TAUFEEK, ta kuma san da ace da wata alaƙa a tsakaninsu ba zata taba aikata haka ba Kai ta girgiza ta kuma juyawa da nufin tafiyarta, a ranta tana yiwa kanta alkawarin wannan ne na karshe, ita ta kawo kanta , da bata zo ba, da bata ga haka ba "Ji mana ai ban gama da ke ba aunty Hajia Khausar!" Yumna ta kuma katse mata hanzari Juyowa ta yi ta sake zuba mata ido, dan kwarai tana so ta ga me kuma marar kunyar zata ce mata? Yumnah ta dubeta ido cikin ido ta ce" Bari ki ji, shigowar ki gidana na nufin yankar tikitin bacin ranki da tashin hankalinki ne, dan a shirye nake tsaf na ja da du wani mai burin ja da Ni, zaki zauna in kin kasance nataciya mai burin son abin duniya, ama a gidan nan sai dai ki min sannu idan ina jinyar ciki in na haihu kuma ku wanken jinnin haihuwa, tsakaninki da wanda yake takamata sai gani sai hange, dama du matsiyaci ya iya kawo kansa inda zai sha wahala, zamu zuba ne, ke kin san kalmar so aka furta min, ke kuwa shishigi ne na keme da masifar son...................................................................... Ido rufe Khausar ta matsewa Yumnah magana ta hanyar dauke gefen fuskarta da mari Wani irin ihu ta saki wanda ya saka TAUFEEK da ya fito daga wajen Khausar din ya ga a rufe karasowa da sauri ya tura dakin dake dan bude ya shigo yana kallon ikon Allah Khausar da har idannuwanta ke neman rufewa ta nunata da yatsa ta ce" Ki kula, harshe mugun nama ne a jikin dan adam, kar tunanin shirmenki ya saka ki kuma zagina koda da wasa ne, dan ban iya zagin iyaye ba sai dai jikinki ya gaya maki!" "KHAUSAR?" Ya furta a nutse yana kallonta Yumnah kuwa wannan dama ita ta fi komai dadada mata, a rikice ta ririke ciki da kai tana ihun cikinta, kanta Khausar ta yi galala tana binsu da kallo domin kansa ta yi ta aniya neman kaiwa kasa Cike da yarda cewar dukan nata ta yi ya tareta ya dauketa ya nufi bakin bed da ita ya kwontar da ita sannan ya mike yana sake bin Khausar din da kallon da ya sakata rasa mene fasararsa ya ce" Kina sane cewar she's prgnt mene laifin da ta maki har zai kai duka?" Wani irin abu na ba zata ne ya zo ya soki zuciyar Khausar wanda tashi daya tana iya kiransa cewa bata so ba TAUFEEK din ya sake goyon bayan Yumnah a karro na biyu , wanda bata taba jin hakan ba, har ta kasa furta masa kalmar A kawai take binsa da kallo A hankali ya sake duban Yumnah dake nade kaffafuwanta tana nishin wahala tamkar wace zata yi bari cikin azabar nan ya sake maido dubansa kan Khausar dake tsaye tana kallonsa da kallon da bai taba ganni a tare da ita ba, domin sun kasance ne idan ya hayayako takan hayayakowa fiye da shi su zuba masifarsu su kuma shirya a tsakaninsu, sai yau ya ga kallonsa kawai take yi Bai yi kasa da gwuiwa ba ya ce" A matsayinki na likita kin san ko wani abu ya hadaki da ita akoy hormone na ciki ko?, Why zaki daketa? Idan wani abu ya samu cikinta fa? , Ya rab me kuke son fara min ne daga hadaku a innuwa daya" "TAUFEEK ya isa dan Allah!" Khausar ta fada tana sakin jakar hannunta kirjinta ba'a dokawa dan gaba daya sai ta ga ya goyi da bayan matarsa ne zai mata wulakanci , bayan a rikici sun yi sama da wannanma bai mata ciwon wannan ba Rai bace ta ce" Bani da hankali ne zan daki cikinta? A kan me zan daki cikinta? An gaya maka ban san abinda nake yi bane?" "Ki rage sautin amon muryarki a kan tawa!" Ya fada a kausashe yana tunkarota Khausar ta rintse ido hawaye ya bale mata tana kallonsa ta ce" Ba zan rage ba, tunda Ni bani da gata sai a wulakantani ko? Ba zan rage ba TAUFEEK, ITANE matar so ko? A kan me zaka hau fada baka bi abinda ya faru ba? Ni sa'arta ce ko tana tunanin haukan da take yi yana gabana ne......... Bata karasa maganar ba ya damki hannunta ya juya da nufin janta, sai kawai ta tubure ta yi kasa da nufin zaunawa a kasa dan babu inda zata bi shi sai dai a yi masifar a nan Ikon Allah ya zubawa ido, bata taɓa tsamatar cewa wai TAUFEEK zai iya jijigarta ya warceta kamar ya warci dan karamin abu a hannunsa sai da ya juyo ya cicibeta ya dagata daga kasa ya juya da Itan ya tura dakinsa ya shiga da ita ya tura da ƙafarsa ta dama sannan ya saukota ya koma wajen kofar ya dana ky ya kuma juyowa kan Khausar wace ke zarro ido tana kallon abin al'ajabi TAUFEEK ne ya daukota kamar ya dauki karamin abu, sai gani ta yi ya nufota gadan gadan Da sauri ta ringa ja baya, dan tsoron da ya shigo cikin kwakwaluwarta yana zuwa zai dauketa da mari ne, dan ba yau ba in dai sunna rikici sai ta yi nesa take masa ihu, a gabansa takan fadi abinda ta ga dama ne ama a sanyaye dan kar yace ta masa ihu A rikice ta rintse ido jin ta hadu da kofar bayi, Da sauri ta bude idannuwanta tana kallon yadda kirjinsa ke bugawa lokacin da ya ce" Na ce ki daina min ihu !" "Taufe...................... TAUFEEK bai bata damar karasa kiran sunnansa ba ya janye hannayenta da take karewa tsakaninsu kamar wani kwarto zai tabata ba mijinta ba, a birkice ya janyota gaba daya jikinsa ba wata wata ya hade bakinsa da nata lokaci daya ya damko harshenta dake masa rashin kunyar a hankali ya rike a cikin bakinsa sai kuma ya lumshe idannuwansa hucin numfashinta na shiga hancinsa a hankali ya sake riƙe harshen sai kumaa cikin dabara ya hade da lebenta a sanyaye ainun ya shiga tsotsa ba tare da ya so aikata hakan a yanzu yanzu ba Mutuwa ce? Ko summa ne? Khausar dai bata duniyar mutane sai ta zazafan abin dake sukan ilahirin jikinta lokaci daya ya bude jajayan idannuwansa ya saka dubansa cikin nata wanda ya sa a rikice ta maida nata duban ta rufe kirjinta na dokawa ama bai bari ba dan fitinaniyar rashin kunya sai da ya gaji dan kansa sannan ya talabata da hannu daya ya sakata a kijinsa ya rungumeta sosai a hankali yana sauke ajiyar zuciya kamar yau ya taba taba leben mace a duniya, muryarsa a shake ainun hancinsa a daidai kitson kanta ya ce" Khausar Please, kar ki rikitani na haike maki bayan ke din yarinya ce....., Khausar plz ki barni na kai wajen da nake son kaiwa idan na yarda cewa eh lalle yanzu *KINA SO NA* , ba hasashe ba......, I beg U kar ki saka na maki gagawa bayan sosai na koyi hakuri a kanki a rayuwata......" Ya Salam........😌🙈🫣kashe TAUFEEK haka kake? Jama'a ya yi sara da mutun sama domin Yumnah itace wace ke makale a kofar dakin tun fitowarsa da Khausar cike da farin cikin son jiyo kukan Khausar din, dan ta sani a kan cikinsa babu abinda ba zai aikata ba😒😏😏😏😏 Cmmnt kari in sha Allah ☹️ [7/22, 5:11 AM] +234 806 670 8178: 💔💔💔💔❤‍🩹❤‍🩹💔💔💔💔 *DA CIWO A ZUCIYATA* 💔💔💔💔❤‍🩹❤‍🩹💔💔💔💔 _MALLAKIN_ *SAJIDA NIJAR* *FREE BOOK NE* 5️⃣1️⃣ *GARABASA, GARABASA, PROMOTION, PROMOTION DIN LITATAFAN MARUBUCIYAR A KAN FARASHI MAI SAUKI 1K, YAN NIJAR KUWA 1000 FRANCS CEFA* 1: Duk karyar kada 2: Yar mahaukaciya 3: Neman na kaina 4: Bani da zabi 5: Bak'a ce 6: Kutkale 7: Makauniya ce 8: Mage 9: Duk nisan jifa 10: Idan ka raina inda kake 11: Dutse 12: Alkalamin kadarata 13: Bani da zabi 14: Dakika Biyar 15:Wata kokowar 16: Aure yakin mata 17: Ni zan ladabi 18: Daga tafia daukar soja *Dukansu a kan farashi mai sauki, zaka saka dubu guda ne domin promotion ne nake yi, ka tuntubeni kan layina kamar haka +227 93 81 16 18, Sajida Nijar* Now *Da CIWO A ZUCIYATA* *Tallah, tallah, tallah* *SECRET DE LA FEMME DU MANGA* _Gidan Kamshi, Sirrin Manyan Mata, nesa tazo kusa,Amarya ,Uwar gida,Ango da mai gida Har ma da yan mata da samari shin kuna sane da cewa HAJIYA FUSAM ta shirya tsaf domin gwangwaje ku da turarakunta masu dankaran kamshi? Tare Kayan gyaram jiki na musamman ,wanda daga nesa kamshin ki kadai ya wadatar ya isar da sakon zuwanki waje,gidan ki kuwa sai ya zam abun kwatance wajen kamshi, kar na cika ku da surutu bara in fara zayyano su_ Farar Humura Bakar Humura Humura special, humura de bain Humura epicé Lait de nuit Parfums désodorisant Parfums rideau et dras Lait de nuit Alkam Kulakcam *Waɗannan kadan ne daga bangaren turaran ruwa* Gagab, sandal flex, Durot, durus, sandal fleur, tafarce, farce, sandal bangui, sandal, hypotonic sandal, al'ut, coktail creation VIP, Gajiji, Mankaji, turaran wutar labule da cafet, Aba malan, boulettes *Munada bangaren gyaran jiki kamar haka:* mai mai saka santsin jiki, mai mai kanshi, Kayan gyaran jiki mai saka fata ta yi santsi da laushi, kayan gyaran jiki mai saka fata ta yi fari, Sabulu mai saka fata ta yi haske, sabulu mai saka fata ta yi santsi, sabulu mai goge yanayin fata, mai wanda baya saka fari mai gyara fata Sayen na gari mai da kudi gida,sai an gwada akan san na kwarai💃💃 Hajiya Fusam na zaune a kasar Niger domin yin magana da ita kai tsaye tuntuɓi wannan number 97 82 44 94 *SECRET DE LA FEMME DU MANGA* Gidan Kamshi, Sirrin Manyan Mata💃💃💃💃💃 Tamkar an zare lakar jikinta haka take ji a irin wannan lokacin, idannuwanta kuwa yadda ka san an saka masu gam ta rufe su ruf, haka kuma jikinta na rawa zuciyarta na dokawa Ya Salam bata taɓa tsintar kanta da jin wata irin nutsuwa mai masifar karfi irin wannan ba, sai idan ta fuskanci alkibla, sai wata irin kunya da tsoro da mamaki da suka mamaye zuciyarta A hankali take jin Hannunsa a bayanta yana dan taping alamun rarashi Tare da rashin karfin gabai Khausar ta nemi zubewa a tsayen da suke Yanzunma bai bata dama ba ya tareta sosai ya kaita har bakin bed dinsa wanda kallonsa kadai abin birgewa ne, ba dan wai ya fi nasu kwaliya ba, a'a, kawai yana dauke da classs ne A hankali ya zauna daf da ita yana jin wani irin abu mai girma na taso masa hadi da nutsuwa a zuciyarsa So yake yi ta bude idannuwanta, ama ta cure waje daya ta rintse ido ta kasa kwakwaran motsi bale har ta bude idannuwan nata "Look at me An mata" ya fada a cen kasan makogwaronsa Khausar ta sake rintse idannuwanta muryarta na dan rawa ta juya ta zubo kaffafuwanta kasa ta mike tana ta sosa keyarta ta ce" Zan je wajen aiki ne, kar, kar kar na makara" Hannunta ya riko ta bayan nan ya maidota, bata shirya ba sai jinta ta yi Dar saman cinyarsa A rikice ta mike tana yaye mayafinta ta juyo tana kallonsa ta ce" TAUFEEK, yau na shiga uku, A'uzubilahi mina shaidani rajim, nice a cinyarka?" Murmushi ya saki na kirki, dan yanzun ya kasa rikewa, sannan ya karewa ɗinkin jikinta kallo ya ce" To a nan waye shedanin ne Matar likita?" Amsa sai ta gagari bakinta ta zuba masa ido tana tunanin yana yi mata haka ne da gaya, dan ya ga tana tsorata dan haka ne yake yi mata, "Bama wannan ba, yau ko Ni ba zan je aiki ba bale ke, zo mu yi fira, kin san irin yadda na yi missing din doguwar fira da ke kuwa? Tunda kika fara zantuka irin na yan maye nake tsoron doguwar fira da ke!" TAUFEEK ya fada yana kallonta, yana matukar jin dadin bakinsa da yadda yake doguwar firar nan da ita, Dama yana fira da ita mai tsayi fiye da kowa a duniyarsa, bale yanzu da yake jin du wata damuwarsa ta kau sai godiyar mai sama Khausar ta yi zaune saman cafet din nan ta rafka tagumi tana kallonsa ta ce" Du kamar ba kai ba, Ni kam yanzu nice na fara rikita a tunanin me yake damunka, TAUFEEK" Fararan kaffafuwansa ya sauko ya zamto yana kallonta a hankali ya furta" kece ke damuna , wai tsaya mema matata ta maki kika daketa?" Khausar ta dago da sauri, ba komai ya sakata dagowa har kamar a firgice ba jin kalmar matarsa da ta yi kai tsaye, Kai ta juyar tana tunanin menene dalilin jin hakan nan da ta yi? "Tell me" ya fada a hankali yana duban yannayin fuskarta kamar daga yannayin mamakinsa ya koma yannayin bacin rai Dago dubanta ta yi, ta sake saukewa a kansa A hankali ta budi baki da nufin fayace masa abinda matarsa tace mata, sai kawai ta ga a kan wani dalili har zata wani fayace masa? Idan ta yi hakan kamar ta hadashi da matarsa ne, dan haka ta dauke dubanta a kansa a hankali ta ce" Zagina ta yi, Ni kuma ba sa'arta bace idan ta kuma zagina zan kuma dukanta ne" "A'a" TAUFEEK ya fada yana hade girar sama da ta kasa Khausar ta sake juyowa tana kallonsa, fuskar a hade ya ce" Aa kar ki dakar min mata, haka kawai? Bama zata kuma zaginki ba, ama da duka ai sai a saka in gigice, Malama kawai kar a wani dakar min matata!" Yana fada yana mikewa ne ya karasa wajen yar karamar wayarsa dake kuka ya dauka ya duba, gannin sunnan Hajia sai ya ajiye wayar ya juyo ya dan saci kallonta, gannin bakinta sai mutsu mutsutu yake yi ya saka shi yin gaba yana yin murmushin da bai bari ta ganshi ba Yana fitowa dakin Yumnah ya koma Yana budewa ya ganta zaune bakin gadonta hannayenta cushe a cikin gashin kanta tana kallon kasa ga wayarta a gefe yashe har madubin wayar a fashe Kai taa dago ta zuba masa ido, zuciyarta na tafarfasa da kunna Bama kamar bakinsa da kuma gangar jikinsa baki daya Zama ya yi bayan ya dauki wayar ya gani eh madubin wayar ne ya yi ratsa ratsa ya juyo zai yi mata magana muryarta cikin kuka ta ce" TAUFEEK, dama kana son Khausar ne?" Idannuwansa ya zuba mata, fuskarsa na dauko yannayin zuciyarsa mai dauke da bacin ran halayan da take nunawa wa'inda sam baya so , kwarai kuma kama sunnansa da ta yi ya bashi mamaki dan rabonsa da ya ji ta kama sunnansa kai tsaye kam shi ya manta A kausashe ya ce" Ban fahimci tamkayarki ba?" Yumnah ta sake zuba masa idannuwanta da suka yi jajajir ta ce" TAUFEEK, dama kana son Khausar ne? Ko me yake faruwa da kai ne?, Na ga ka saka hannu ka dauki Khausar kuma ka kaita dakinka ka haɗa jikinka da nata?" "Labe kika min ne?" Ya furta yana son tabatarwa Yumnah ta yi tsuru tsuru ta kasa bashi amsar tambayar da ya yi mata Rai bace ya ce" Saurara, ki kula, bana son shashanci Yumnah! Tambayar ina sonta ko bana sonta bai shafeki ba, amsar da nake so ki sani shine ki koyi zama da ita dan ba zan iya zama babu ita ba!, Ki kuma kiyaye yi min ciwon karya dan kar na kirki ya kama ki a ki yarda har ki yiwa kanki ila, labe kuwa idan shi zaki min fine, zaki hanna kanki da kanki ne!" Yana gama fada ya mike ya yi tafiyarsa, ya barta zuciyarta tamkar zata fito ta bakinta irin yadda take bugawa, gashi wayarma da zata yi kiran Mamanta ta fasa, innalilahi Wa inna ilaihi raj'une bata haduwa da bugawar zuciya irin ta yau ba, nan da nan kanta ya dauki ciwo ta kwonta a nan tana gursheken kukanta, domin bata san yaya zata yi ba, ina zata saka ranta, lalle namiji namiji rigar kaya! TAUFEEK kansa kan nasa ciwon yake yi masa sosai A cikin zuciyarsa yana yin iya kokarinsa dan gannin ya kiyaye bata ransa a komai Ama yana tsoron Yumnah da sababin halayan da take nunawa, ace ta nuna sumar karya, ta ringa zaburar karya dan ta hannashi kasancewa da iyalinsa? Baya so ya kai wajen da zai nuna mata shine mijinta kuma miji ga Khausar,, babu ɗaya da ta isa ta hanna shi kyautatawa daya dan shi ba solofiyon namiji bane Yana fitowa da nufin zuwa bangaren Mai kwanoni ya kuma saka masu aiki a kawowa su KHausar abinci dan bai ga alamun wani zai girka ba ya yi turus gannin Hajia zaune da Hamdiya sai fada take yi tana fadin wannan ai wulakanci ne a sakawa baban falo sakata Tunda ya fito ya yi turus din itama ta mike tana kare masa kallo daga kasa har sama, sai kuma ta yi wani dan murmushi ta ce" Magidanci sai yanzu aka sauko?" Fuska ya hade ya ce" Daga ina?" Hajia ta ce" Daga sama mana inace dakinka a sama yake?" TAUFEEK ya tabe baki yanna kallon kwondon dake tare da su ya ce" Me kuke nema a nan da safiyar Allah?" Hajia ta dan zarro ido tana fadin" Elhaji karami karfe tara ta gota fa,, kuma abin kari na je aka yi na kawo shine nake ta kiranka baka dagawa me kake yi a cikin ne haka?" Ido ya zuba mata, tunani yake yi to shi anya ba ya shiga uku ba kuwa? Subahanalahi shin me wannan matar ke so da shi ne? Hade fuskar ya sake yi ya ce da Hamdiya" Ke ajiye ki bace a nan" Da sauri ta ajiye ta juya har kamar zata kifa ta nufi cen bangaren iyayen TAUFEEK kuwa ya zubawa Hajia ido, shi walahi sai ya rasama me zai mata Zagayeta ya yi ya yi tafiyarsa, ba zai iya ba sam, baban takaicinsa da yace mata yana iya Bara mata gidan tsaf ta hada taron iyayensa aka tabatar masa ko gidansa zai kaura da ita zai je, sai kawai ya sarewa duniya ya san ita din wata rikicin duniyarsa ce Da ido ta bi shi har ya bacewa ganninta ta tabe baki ta tura kofar ta shiga tana haki da katon kwondon nan Tana shiga ta ringa salama sama sama, sai a kan kunnen Khausar wace take zaune ta cika taf tamkar zata fashe ta mike tana amsawa ta dauki mayafinta ta yafa ya rufe kanta da jikinta sosai sannan ta fito ta sauko yana amsawa hadi da sakin fuskarta sosai ta duka tana gaishe da Hajia Hajia ta zuba mata ido, sai kuma ta dafe haba cike da takaici ta ce" Aikin banza da na san garas kike babu mai sakani yi miki abincin safe, ku dai an yi shashashu walahi, na tabata bai ji gargadina bane, yaron nan so ake a shiga gabansa, dole in tashi tsaye, in ba lalaci ba irin na magidanci yau kwana bakwai da aka zarga maka nace har mace a wuyanka ama ka iya kwontawa ka tashi ras tana tafiya lafiyar Allah a gaban ka? Ko dai bashi da lafiya ne Ni dije?" KHausar ji take dama kasa ta bude ta shige ta huta da lamarin Hajia, To ita me zata cewa Hajia ne jama'a? Innalilahi wayo wayo tashin hankali "Kin yi shiru khausara,, kin ga taso karya in ji ke din wani lalaci ya sa kika zuba masa ido bayan halal ne kuma wayo ne mace ta nuna ta san ciwon kanta ? Maza karbi ci in ji " Hajia ta fada tana loda mata abinci a plate, ba tare da ta damu tambayar inda Yumnah take ba, dan kwata kwata bata saka a ranta cewa zata samu arzikin gaisuwa daga yarinyar ba, domin kuwa du irin mugun kallon da take yi mata bata boyewa a kan idannuwanta ne, shi yasa gaba daya yarinyar ta fice mata a rai, ai ko ba komai sai ta girmama tsufanta, ama tana abu kamar babu manya a gidansu ko ba'a koya mata bin na gaba ba, walahi bata taɓa tunanin mahaifin Yumnah yana da mutunci har haka ba, ko a jiya fa ta san abinda zai faru kennan da bata yi yade yaden maganar nan ba, ama tunda Baba ya sanar mata mahaifin Yumnah na so a zauna sai ta saka a ranta shima zai zo ya ki sauraron kowa ne ya zubda rashin kunya, shi yasa ta zo a shirye a jiyan sai ta ga mutun mai mutunci da daraja wanda ke so y'arsa ta yi zaman aurenta cikin salama, fatanta Allah ya daidaita wannan lamari, ama bata tunanin zata iya jituwa da fitsarar Yumnah sam, kuma ta tsaya tsai a kan kaffafuwanta sai inda karfinnta ya kare a zamantakewar magidanci da Khausar, dan ita ta jima da Sannin cewa Khausar itace zuciyar jikanta, abinda bata sani ba shine menene dalilin da ya sa ya kasa neman aurenta a kulun sai dai ya je ya zube saman kujerar ta ya yi ta huci idan wani abu da ya danganci soyyayar Khausar din ya shiga kunnensa, Khausar ta karya daidai misali, Hajia ta shake mata tsumin da ta hada da kanta ta mika mata tana fadin" Maza shanye maganin basir da maiko maikon mara ne , in kana shan wannan fa da kika gani ko al'ada zaka yi baka jin ciwo " Khausar da mamaki ta ce" Kai Hajia? Wannan din? Kin ga kuwa nakan ji ciwon al'ada sosai magani nake sha du idan zai zo" Hajia ta gyara zama ta wani saki murmushi ta ce" ke magungunan nan ai sai su tarun maka ciki , ya zamana ko wani wata sai ka makari magani ko zaka iya mikewa? Daga yau ga sauki Allah ya kawo sosai ki sha kawai ki kuma ajiye daf da gadonki ki ringa sha ga kuma madara sabuwar tatsa kin san magidanci na kiwo a bayan gida ana kawo min kulun da asubahi shine na yan maki" Zuciya Na son mai kyautata mata, Hajia yada zango ta yi suke fira hankali kwonce da Khausar tamkar jikarta ta jinninta har goma ta gota sannan ta mike ta yi tafiyarta bangarenta A bangaren TAUFEEK kuwa a fitarsa ya gana da mahaifinsa sannan ya samu Alhusain dake bangaren baki dan a nan ya kwana ya yada zango suka shiga fira kadan kadan sunna fitar abinda ya shafe su sai kuma Alhusain ya yi murmushi cike da shakiyanci ya ce" Yaya kwanan Besty dinmu?" TAUFEEK ya zuba masa ido, sai kuma ya dauke ya masa banza Alhusain ya ce" A jiya, da aka hanna mana Besty dinmu yaya zaka yi? " TAUFEEK ya yi murmushi yana girgiza kansa ya ce" Rigima kake nema?" Alhusain ya girgiza kai ya ce" wane mutun, Ni in nemi rigima da mai fuska biyu? Kai fa ka ga a wajen aiki aikinka kala biyu ne, a gaban Aba kai yannayinka biyu ne domin a gabansa salihi marar fada haka kake ama a waje idan ka samu wajen yi har tubewa kake yi, kuma ka ga haka besty dinmu ma kake mata a gabanta kai besty ne ama a zuciyarka ba hakan bane, kai kam kana fama, Ni ina zan iya , ba zan iya ba ko kadan man!" TAUFEEK ya sauke ajiyar zuciya , a hankali ya dafe gaban goshinsa yana rintse idannuwansa da tuna irin fargabarsa da tashin hankalinsa A hankali ya ce" Nima na kusa mutuwa Man" Alhusain ya zarro ido yana kallonsa ya ce" Mene?, Rashin lafiya ka yi ne?" TAUFEEK ya yi murmushi mai daci yana gyara zamansa daga kafa daya kan daya ya maida kaffafuwan a kasa yana kallonsa ya ce" Man, da ban mutu Bama da na hadu da jinya, ka san saura kiris yarinyar nan ta auri wani ko habu ko Murtala? Ni sunnan bace min yake yi dan a kulun in ta fadi sunnan sai in ga kamar wani la'antacen sunna" Dariya Alhusain ya fashe da ita, dan walahi irin yadda TAUFEEK ya yi harda dantse lebe ya tabata da ya hadu da wannan mutumen a yanzuma sai sun raba hali Yana dariya harda saukowa daga saman kujera yana kallonsa ya ce" Kana da akida mai tsauri abokina, tunda ka gabatar min da ita na gane nima halin da kake ciki, na rikitaka ainun ama ka ki ka fada mata, duba ka ga ranar aurenka ka yi kiranta murya a shake , burinka ta zo daf da kai, ka ga tunda na ga ka iya sakama kanka irin wannan rikicewar zuciyar na san du wanda ya taboka tsaf zaka hargitsa shi, why zaka rayu da ciwo a zuciyarka tsayin shekaru?" "A kanta ina da tsoro mai girma Man kaima ka sani, tsorona daya ne tall a wayi gari dan na kasa rike abinda ke raina in rasa zumuncinta, ka san yarinyar nan kallon sako take min?, Kuma tana iya zama ta fada min sirinta, na shaku da hakan ainun, kai bari ka ji da an aura mata wani da mun yi mutuwar kasko !" "Abokina idan akoy boyayan mutun bayanka ne, ka dai bi min besty a hankali!" Alhusain ya fada yana sake yiwa TAUFEEK dariya Taufeek ma ya yi yar dariya yana girgiza kai ya ce" Ya danganta , kuma ka daina ce mata besty, babu abota tsakanin namiji da mace sai Ni da ita kadai!" ( To ba kun ji ba?) .......................im sorry people ina busy ne ga weekend Na gode 😍😍😍🙄 [7/24, 10:04 AM] +234 816 049 3429: 💔💔💔💔❤‍🩹❤‍🩹💔💔💔💔 *DA CIWO A ZUCIYATA* 💔💔💔💔❤‍🩹❤‍🩹💔💔💔💔 _MALLAKIN_ *SAJIDA NIJAR* *FREE BOOK NE* 5️⃣3️⃣ *GARABASA, GARABASA, PROMOTION, PROMOTION DIN LITATAFAN MARUBUCIYAR A KAN FARASHI MAI SAUKI 1K, YAN NIJAR KUWA 1000 FRANCS CEFA* 1: Duk karyar kada 2: Yar mahaukaciya 3: Neman na kaina 4: Bani da zabi 5: Bak'a ce 6: Kutkale 7: Makauniya ce 8: Mage 9: Duk nisan jifa 10: Idan ka raina inda kake 11: Dutse 12: Alkalamin kadarata 13: Bani da zabi 14: Dakika Biyar 15:Wata kokowar 16: Aure yakin mata 17: Ni zan ladabi 18: Daga tafia daukar soja *Dukansu a kan farashi mai sauki, zaka saka dubu guda ne domin promotion ne nake yi, ka tuntubeni kan layina kamar haka +227 93 81 16 18, Sajida Nijar* Now *Da CIWO A ZUCIYATA* *Tallah, tallah, tallah* *SECRET DE LA FEMME DU MANGA* _Gidan Kamshi, Sirrin Manyan Mata, nesa tazo kusa,Amarya ,Uwar gida,Ango da mai gida Har ma da yan mata da samari shin kuna sane da cewa HAJIYA FUSAM ta shirya tsaf domin gwangwaje ku da turarakunta masu dankaran kamshi? Tare Kayan gyaram jiki na musamman ,wanda daga nesa kamshin ki kadai ya wadatar ya isar da sakon zuwanki waje,gidan ki kuwa sai ya zam abun kwatance wajen kamshi, kar na cika ku da surutu bara in fara zayyano su_ Farar Humura Bakar Humura Humura special, humura de bain Humura epicé Lait de nuit Parfums désodorisant Parfums rideau et dras Lait de nuit Alkam Kulakcam *Waɗannan kadan ne daga bangaren turaran ruwa* Gagab, sandal flex, Durot, durus, sandal fleur, tafarce, farce, sandal bangui, sandal, hypotonic sandal, al'ut, coktail creation VIP, Gajiji, Mankaji, turaran wutar labule da cafet, Aba malan, boulettes *Munada bangaren gyaran jiki kamar haka:* mai mai saka santsin jiki, mai mai kanshi, Kayan gyaran jiki mai saka fata ta yi santsi da laushi, kayan gyaran jiki mai saka fata ta yi fari, Sabulu mai saka fata ta yi haske, sabulu mai saka fata ta yi santsi, sabulu mai goge yanayin fata, mai wanda baya saka fari mai gyara fata Sayen na gari mai da kudi gida,sai an gwada akan san na kwarai💃💃 Hajiya Fusam na zaune a kasar Niger domin yin magana da ita kai tsaye tuntuɓi wannan number 97 82 44 94 *SECRET DE LA FEMME DU MANGA* Gidan Kamshi, Sirrin Manyan Mata💃💃💃💃💃 A nutse Husaini ya yi masu takaitaciyar nasiha irin wace ya dace ace ya yin a matsayinsa na aminin kusa da TAUFEEK din Bai wani ja dogon Zama ba ya nuna zai tafi, nan Khausar ta mike tana fadin" Ina zuwa Besty" Ta juya ta haye sama, shi kuma ya kalli TAUFEEK yana masa murmushin shakiyanci dan Khausar ta ce masa besty Jim kadan ta sauko hannunta rike da wata bakar leda mai sirri, ba komai bane a ciki sai yan kannanun humura masu dadin kanshi da saka nutsuwa ta bada tana fadin sakon madame ne sannan ta koma ta zauna Har ga Allah bata yi haka dan ta birge TAUFEEK ko dan ta ba matarsa haushi ba, a ranta ta ji ya dace ta yi hakan dan tana da damar hakan, ko a da idan ya zo takan daka su kuli, su miyar Hausa da yajin dadawa ta bada a kaima madame, yanzun kuwa gannin bata da su sai ta bada humura dan ta san itama abu ce da take iya birge wanda ke kasar waje Sai dai wannan kokari nata ya matukar birge TAUFEEK duda ba yau ta fara ba, matarsa kuwa sai ta ga kamar wace ta yi da gaya dan ta bata mata, ita dai tana zaunenta har ya mike suka tafi Yumnah sai addu'a take yi da fadin a turo mata numbar madame din sa ringa gaisawa idan ta sake waya , shi dai Husaini ya yi godiya sosai kafin ya fice TAUFEEK ya sanar masa yana zuwa dan sai ya kaishi aeroport du kuwa da irin yadda ya ki ama yace sai ya kai shi Dawowar da ya yi ba ta komai bace sai ta tsokana da son cinma burinsa cikin ruwan sanyi Zama ya yi a saman kujerar yana fadin" Wai yau me zan ci ne? Wifeyyyyyyy" Har ga Allah ita ta kalle shi ne ba dan ta saka a ranta da ita yake ba, sai kuma gannin ba ita yake kallo ba ya saka ta zuba masa ido a ranta tana jin to wai wannan kamar an cin mata fuska ko ana daf da raina mata hankali Yumnah kam wani sanyi ta ji a ranta, cike da rage murya irin karma a ji tan nan, irin maganar nan ta wasu matan idan sunna yiwa miji a gaban kishiya cike da kisisina ta munafurci ta ce" Oh sorry my hero, yau baka ci komai ba? Bari in shiga kicin in sama maka wani abin" TAUFEEK ya yi dan murmushi har ta mike tana layi dan ba fa karfin jikinta take ji ba ya riko hannunta yana kallonta ya ce" A'a, a haka ba zaki iya girki ba, bari idan na fita in shigo mana da shi, zan raka Husaini" Yumnah ta dawo ta dane cinyoyinsa ta dora kanta a kirjinsa, nan ne kuma Khausar ta mike dan ta kula ana daf da aikata rashin mutunci a gabanta ta juya da dan sauri bayan ta warci kaskon turaren wutarta ta haye sama tana jin wata tafarfasa da ranta ke yi ta kai ta ajiye kaskon ta kashe wutar sannan ta ringa kai kawo cike da jin wani haushi a ranta kafin ta nemi waje ta zauna tana karkada kafa cike da jin kewar iyayenta yau har kwana na biyu bata ji su ba, bata da waya, ga wayar nan layin baya ciki, kuma babu litatafanta daga ita sai ranta dan ko Alkur'ani babu a dakin nata bata san ba kuma akoy wajen Ajiyesu a falon masu yawan gaske ma kuwa bale ta dauko ta yi karatu, sai kawai ta ringa sake sake har ta ji ranta na tafarfasa yana bacewa sosai kan irin abinda TAUFEEK ke yi mata a gidansa Kwonciya ta yi tana ta huci har ta dauki lokacin da ita da kanta bata sani ba sai da ta ji bude kofar nata ta mike da sauri dan bata san cewa bata rufe dakin ba ta dago ta zuba masa ido Yanzun bata da hijab din rigar ce kawai a jikinta, kuma bata da rigar mama sai kafecen pant dinta a kasan rigar wanda tsaf ya bi sawun rigar tunda ba yar a rufe asiri bace mai santsin nan ce kuma link color ya zamto harta zannen yan mulalan Mamanta ana gani tsaf ga wanda ya kalla dan ya gannin Ledojin dake hannunsa ne suka so kubcewa daga hannun nasa Da kyar ya iya tarewa ya rike yana dan dafe bango kadan daga makogwaronsa kuwa yana fitar da wani irin huci mai dumin gaske ya sake zuba mata ido Da kyar ya cira tafiyarsa ya karaso inda take tsaye ta rike kugu tana sakar harare gefe da gefe Ajiye ledojin ya yi ya dago ya sake zuba mata ido Dukkan alamu na masifa sun bayyana a tare da ita, wa'inda sam bai so ganninsu a yanzu ba, bai san dalili ba, harma yake daf da manta abinda ya yi mata take fushi Ledar ya juya ya kalla ya sake juyowa yana kallon yadda kannanun kitsonta suka wani yarfu abin dai ba'a cewa komai ya dan yi gyaran murya dan maza ne ai kar ya bada kansa a tausashe ya ce" taho mu ci abinci Khausar" Ledar ta bi da kallo zuciyarta na mata wani irin tukuki A hankali ta maida dubanta kansa, yanzun bata daga murya irin na dazu ba, ama a sanyayen sai ya ji inama Muryar ta daga yadda zasu yi ba dadin A hankali ainun Khausar ta samu kanta da fadin" Ni acici ko? Taufeek Ni acici ko? Bana ci barci nake ji" Daga haka ta karasa bakin bed dinta a nutsen da bata san tana da nutsuwa har haka ba ta hau gadon ta juya bayanta ta kwonta tana janyo abin rufa a hankali ta rufa jikinta da shi Tunda ta bashi baya har ta kwonta din kallonta yake yi yana tunanin me yake faruwa ne? Me ya sameta ne? Ko bata da lafiya ne? Dayar ledar mai dauke da kwalin wayarta wace yanzun ya ajiyewa Yumnah Tata da abincinta kafin ya mata salama ya shigo nan din ya dauka ya karasa a hankali bakin gadon yana mika hannunsa ya yaye rufar a hankali ya ce" Hey, menene? Waye ya taba ki? Taso in ji waye ya bata maki rai?" Khausar dake boye hawayen dake neman tarun mata a idannuwanta a hankali ta girgiza kanta tana rike abin rufar ta ce" a'a babu wanda ya bata min TAUFEEK barci ne nake ji Please " Wani irin tashin hankali yake jin zai damu zuciyarsa, har ya kasa ciro wayar tasa Khausar ta dan juyo tana kallonsa kasa kasa ta ce" Ka tashi in rufe dakin dare ya yi " Dakin ya bi da kallo, a hankalin shima ya samu kansa da fadin" Ni kuma fa, in kwana a ina?" Khausar ta maida idannuwanta ta rufe tana ji kamar tace masa ka je dakin matarkan mana, sai kuma ta kwabi kanta ta ce" Ai dai ba a nan ba zaka kwana ko?" TAUFEEK ya mike tsaye yana fadin" A ina kike so na kwana?, Bari in dauko computerna kar ki rufe min daki" Samun kanta ta yi da bin bayansa da kallo kafin ta maida idon nata a hankali ta rufe tana jin ta kasa mikewa ta rufe dakin, ko kuma bata so ta rufe din ne? Kai kamar wace take gudun ta rufe din ya je wancen dakin ya kwanan, haka kawai take jin idan ta yarda aka yi mata haka kamar an wani wulakantata ne ai! Sai kawai ta lumshe idannuwanta tana sauraronsa har ya dawo din ta sake yin shiru tana sauraron dan motsinsa kadan kadan har ta ga ya hayo gadonta, hakan ya sa ta dan dago tana kallonsa sai ta ga sam bai dubeta ba ya dauko filo yana jerawa a tsakaninsu har kusan kafafuwa sannan ya tafi cen karshen gadon ya wani rabe da computarsa ya yi kamar bai san tana kallonsa ba ya shiga aikinsa yana waya hankalinsa a kan wayar gaba daya A hankali ta kara komawa tsinin gadon ta makure jikinta kwakwaluwarta cike da tunanin to yaushe zai saukar mata a gado? Tun tana hangen bayansa da jiran gannin ya saukar mata a gadon har barci ya ringa fizgarta gaba daya ya dauketa jikinta ya saki sosai idannuwanta a lumshe ta yi filow da dayan hannunta dayan kuma yana daf da abin rufar ta sake shi da barcin ya dauketa A hankali ya ajiye computarsa sannan ya juyo ya ringa janye filo din yana sauke su gaba daya daga gadon, dan bai ga amfaninsu ba, sam basu da waje a gadon nan Yana gamawa ya sauka ya je ya kashe fitila sannan ya hayo saman gadon ya kwonta ya haska yar karamar wayarsa ya zubawa fuskarta ido Kasa kasa sosai ya ce" Khausar, my dream, my life, ......" Idannuwansa ya lumshe yana jin nutsuwa na shiga zuciyarsa, a hankali ya matsa bayan ya cire rigar jikinsa ya janyota jikin nasa ya rungumeta ya zamto rabin jikinta a saman kirjinsa ya zagaye sauran jikin nata da hannunsa ya tofa mata adu'ar barci ama shi masa barcin ya ki zuwa da salama kamar yadda ita ta samu Bukarta yake, so yake yi ya ji lebenta a saman nasa ta yadda zai iya samun nutsatsen barci Sai dai kashhhh Ba zai yi mata gagawa ba, ko a haka ya san ya godewa Allah ya samu wani baban abin daga ita bayan dogon jira da cire tsamani A hankali barcin shima ya dauke shi, har ya ji karancin barcin a lokacin da kiraye kirayen asubahi suka farkar da shi ya zubawa fuskarta ido gannin yanzun itace ta masa riko irin na filo tana barcinta hankali kwonce A hankali ta fara alamun motsawa saboda kiraye kirayen sallah, shi kuma ya ki sauketa a jikinsa dan yana so ta farka ya ga reaction dinta Idannuwa ta fara budewa sannu sannu kafin ta laluba hannunta a inda yake ajiye daf da gemunsa Lalubawa ta sake yi tana mai tabatarwa kanta eh lalle gemu gashi ne dan haka da sauri ta dago idannuwanta suka shiga cikin nasa Ido ta zarro , shima ya zarro nasa ta mike da sauri tana kale kale shima ya zuba mata ido a dole sai ya ga gudun ruwanta, ai kuwa ta kawar da kai salatinta ya fito fili ta mike da sauri ta yi bayi tana wartar hularta ta ja ta rufe sai zarro ido take yi Murmushi ya saki ya sauka a gadon ya dauki rigarsa kadai ya saka ya fice shima a dakin hankali kwonce ya nufi nasa dan zuwa Masallaci Ko da ya dawo daga masallaci ya je dakin Yumnah 6a tarda ita ta koma barci dan bata samu barcin ba duka daren sai ya fito a hankali ya je dakin Khausar din ya bude ya shiga da salama sannan ya sauke dubansa a kanta tana saman salaya da farin carbinta tana ja Kai ta sake sinewa tana jin wai ita da ina zata fara da abin kunyar nan jama'a? Ya karaso a hankali bayan ya dauko karamar wayarsa ya zauna daf da ita, bai ce mata komai ba ya janyo hannunta ya rike cikin nasa hakan ya sa ta sake sinne kai shi kuma ya ki yin magana har sai da ta gaji da kyar ta iya budar bakinta yana rawa rawa ta ce" Ina kwana" Murmushi ya yi ya ki amsawa, sai da aka jima ya ce" Lafiya, " Wajen ya sake daukan shiru, a hankali ta dan dago dan yin magana wayarsa ta katse mata maganar ya daga a tausashe ya yi salama a nutse ya gaisar da Mama ta hanyar fadin" Barka da safiya matar mai kwanoni" Mama ta amsa shi ita dinma a nutse sannan ta ce" Dama, dan na ji ne idan da hali ka zo ka duba min Hajia da na zo gaishe da ita na sameta ba lafiya " Wani irin firgita ya yi daga yannayinsa na nutsuwar nan yana wara idannuwansa da dan sauri ya ce" Hajiar? Me ya sameta? Ganinan zuwa" Daga nan ya mike da gagawa yana fadin" Ina zuwa Hajia ce ba lafiya" Mikewar ta yi itama ta take masa baya tana fadin " Subahanallah yaushe?" Shi kam gaba daya magana ya kasa saima da ta tuna masa bai dauki abin dubata ba sannan ya nuna mata dakin nasa kan ta dauko dan sai ya kasa komawa saman Da saurinta ta karasa bangaren Hajiar a lokacin TAUFEEK na zaune a saman kafet ya dora kan Hajia saman cinyarsa yana rike da hannunta daya cikin nasa yana tofa mata addu'a, gefe daya kuwa Baba ne ke kai kawo da carbi a hannunsa kana kallonsa zaka gane hankalinsa a kololuwar tashe yake, sai matansa biyu dayar na ba yaronta nono dayar kuwa tana zaune da carbinta a hannunta Khausar ta shigo ta gaishe da kowa a jimulce daidai lokacin da Mama ta fito daga dakin na Hajia ta gyara shi tsaf ta dubi TAUFEEK da yan kurumcin suka tashi sakamakon ciwon Hajiar ta ce" yauwa dan gyara mu maidata ciki sai ka dubata " Taufeek ya sake kallon fuskar Hajia, wace idannuwanta ke rufe a hankali ya dago ya kalli mamansa ya ce" *Mama*, ba zan iya barinta a nan ba , kin san da ba hutawa zata samu ta yi ba, bayan mai dauke da ciwo irin nata yana da bukatar hutu lokaci zuwa lokaci na kirki" Mama ta gyada kai ta ce" To tashi mu kamata a je asibitin ko" Ajiyar zuciya ya sauke ya sauke kanta a hankali yana kallon KHausar ya ce" Tana da diabete da kuma hawan jinni, nd tana da wani ciwon kai dake tasar mata lokaci zuwa lokaci" A hankali Khausar dake gyara mata hijabinta ta gyada kanta ta gyara Mama ta karaso sosai suka kama Hajia wace kuwa ke kwasa idannuwanta kuwa a rufe saboda ciwon kai suka talabata ita da Khausar shi kuwa ya shige ciki dan daukar mata abubuwan da ya san bata rayuwa sai da su dan tana iya dawowa da zarar Allah ya sa ta dawo a hayacinta saboda su Yana daukowa Baba na amsa ne har suka gama fidowa suka shiga Mota daya shi da TAUFEEK din suka nufi asibitin domin tuni su Mama sun yi gaba da direba Sunna isawa ya tarda tuni an karbi Hajiar an rufu a kanta domin akoy litafinta a nan komai a rubuce da abinda ke kawota asibitin, shi suka fara aunawa sannan aka shiga wasu aune aunen dan haka sai ya samu waje ya yi tsaye kawai yake addu'a zuciyarsa na rawa ainun Baba dake zaune shima kansa a dafe ya dago ya ce" Wai wani abu aka yi a gidan da ya daga mata hankali ne? Na ga ta jima rabonta da wannan ciwo?" Mama ta juyo inda yake zaune, sosai take jin damuwarsu a zuciyarta, sai dai ita dinma a cikin damuwar take na ciwon Hajiar, domin Hajia ita uwa take a wajenta Bama sarakuwa ba, a sanyaye ta ce" [7/24, 10:04 AM] +234 816 049 3429: 💔💔💔💔❤‍🩹❤‍🩹💔💔💔💔 *DA CIWO A ZUCIYATA* 💔💔💔💔❤‍🩹❤‍🩹💔💔💔💔 _MALLAKIN_ *SAJIDA NIJAR* *FREE BOOK NE* 5️⃣2️⃣ *GARABASA, GARABASA, PROMOTION, PROMOTION DIN LITATAFAN MARUBUCIYAR A KAN FARASHI MAI SAUKI 1K, YAN NIJAR KUWA 1000 FRANCS CEFA* 1: Duk karyar kada 2: Yar mahaukaciya 3: Neman na kaina 4: Bani da zabi 5: Bak'a ce 6: Kutkale 7: Makauniya ce 8: Mage 9: Duk nisan jifa 10: Idan ka raina inda kake 11: Dutse 12: Alkalamin kadarata 13: Bani da zabi 14: Dakika Biyar 15:Wata kokowar 16: Aure yakin mata 17: Ni zan ladabi 18: Daga tafia daukar soja *Dukansu a kan farashi mai sauki, zaka saka dubu guda ne domin promotion ne nake yi, ka tuntubeni kan layina kamar haka +227 93 81 16 18, Sajida Nijar* Now *Da CIWO A ZUCIYATA* *Tallah, tallah, tallah* *SECRET DE LA FEMME DU MANGA* _Gidan Kamshi, Sirrin Manyan Mata, nesa tazo kusa,Amarya ,Uwar gida,Ango da mai gida Har ma da yan mata da samari shin kuna sane da cewa HAJIYA FUSAM ta shirya tsaf domin gwangwaje ku da turarakunta masu dankaran kamshi? Tare Kayan gyaram jiki na musamman ,wanda daga nesa kamshin ki kadai ya wadatar ya isar da sakon zuwanki waje,gidan ki kuwa sai ya zam abun kwatance wajen kamshi, kar na cika ku da surutu bara in fara zayyano su_ Farar Humura Bakar Humura Humura special, humura de bain Humura epicé Lait de nuit Parfums désodorisant Parfums rideau et dras Lait de nuit Alkam Kulakcam *Waɗannan kadan ne daga bangaren turaran ruwa* Gagab, sandal flex, Durot, durus, sandal fleur, tafarce, farce, sandal bangui, sandal, hypotonic sandal, al'ut, coktail creation VIP, Gajiji, Mankaji, turaran wutar labule da cafet, Aba malan, boulettes *Munada bangaren gyaran jiki kamar haka:* mai mai saka santsin jiki, mai mai kanshi, Kayan gyaran jiki mai saka fata ta yi santsi da laushi, kayan gyaran jiki mai saka fata ta yi fari, Sabulu mai saka fata ta yi haske, sabulu mai saka fata ta yi santsi, sabulu mai goge yanayin fata, mai wanda baya saka fari mai gyara fata Sayen na gari mai da kudi gida,sai an gwada akan san na kwarai💃💃 Hajiya Fusam na zaune a kasar Niger domin yin magana da ita kai tsaye tuntuɓi wannan number 97 82 44 94 *SECRET DE LA FEMME DU MANGA* Gidan Kamshi, Sirrin Manyan Mata💃💃💃💃💃 Da mamaki Alhusain ya ce" what? Babu abota tsakanin mace da namiji? Abokina ama baka da mutunci, ai kai ka yi?" TAUFEEK ya kare masa kallo ya dauke kai yana duban abinda ake watsowa a tv ya ce" Haramun ne ai, kuma Ni ban ce abota nake yi ba ku kuka ce, man tashi mu je mu dawo mana kar na bar amana ita kadai" Yanzun kam Alhusain rasa bakin magana ya yi, ya mike ya bi bayansa yana tunanin babu wanda ya raina shi kamar TAUFEEK, ama ba komai shi ya san in dai a kan lamarin Khausar babu wanda ya bari Sosai TAUFEEK ya wuni cikin sukunin zuciya , sai da yama ta yi likis suka dawo Alhusain da niyar zai wuce ne karfe goma sha biyun dare zuwa kasarsu, dan haka suka yi da amininsa idan suka fito daga wajen su Hajia zai shiga ya yiwa su KHausar nasiha Sun tafi wajen Mama ya yi mata salama, ta bashi sako ya kaiwa matarsa , daga nan ya yiwa su Hajia salama wa'inda suke falo sunna kallo Sunna fitowa suka yi bangaren Hajia , wace ke zaune tana gyaran asuwakinta Sosai suka taba fira ta dauko masa turaran wuta na jiji tari guda ta bashi tana kallonsa ta ce" Kai ashe mace daya ce da kai ko? Ka ga raba biyu kawon rabi kai mata rabi, da su biyu ne sai ka kai mata su raba ama daya kwal uwa rai ina Ni ina dumbuza wannan turare mai albarka?" TAUFEEK ya karbe yana sakar mata harara ya ce" Bani nan, ke kam Hajia ban san yaya zan yi da ke ba, sai an kai mata dukan , wannan abin mai kauri mema zai yi da shi amshi abinki!" Alhusain ya rike yana girgiza kai ya ce" Turaran Hajiar ne mai kauri? Ni tunda nake na taba jin turare mai albarka irin wannan? Kanshinsa fa in ya shafi suturarka har a wanke yana nan daram babu inda yake zuwa bani ina son abina" Hajia ta wani saki murmushi tana kallon Alhusain ta ce" ka ji na Allah mai fadin abu domin ALLAH, kai shima fa sunnan an masa auren ne dazu da na kaiwa Khausara tuwon kari ras ta zo ta ansa ta shaki tuwona , haushi yadda ka san in dagawa magidanci nono kowama ya huta, wannan mugun hali da me ya yi kama, a baka y'ar a wanke tasss a gyare tana kanshi tana MUSMUS komai a wadace yana aiki irin wanda basa jin tsoron Allah, ka masa nasiha in kuma bashi da lafiya ne a sanar min in tashi tsaye dan da ka ga magidanci gaba da baya makiya ne da shi, matan uban nan kamar su kashe shi suke ji, kar su harbi lafiyarshi in shiga uku!" Fada take yi tamkar ta ari baki, Alhusain kunya da dariya kamar su kashe shi kansa a kasa ya dantse lebe, TAUFEEK kuwa ya zuba mata ido yana kallo kamar wata sabon gani sai da ta dasa Aya ta sakar masu ledar turaran jijin tana turo baki hadi da gyara hijabinta TAUFEEK ya girgiza kai cike da haushi ya ce" idan na kuma gannin kafarki a bangarena tabas sai na san yada na yi da ke, ke kam Hajia sai addu'a kuma, kar na kuma ganninki a wajena dan tsaf kike iya zige min mata , ku ji hijab har kasa kamar wata Malama , kuma da yake cewa turaranki dadi yana nufin kaurinsa idan kika turarawa mutun har ya yi wanki basa fita Ni koma kar ki biyo mu meye kike saka takalmi?" Alhusain ya zarro ido yana fadin" kai da Maman Baba kake? Lalle baka da kunya, kuma bestyn kake kira matarka a gaban Hajia? Sai ta bi mu ai nasiha zamu yiwa matanka nasiha kuma da manya ta fi , mutumen kawai Hajia ai babu malamin da ya kaita kake wani yi mata rashin kunya" Hajia ta ce" Gaya masa, gaya masa dan nan, Ni banma san me na masa ba da magaribar nan yace ba zan bi shi ba, wai kar na je bangarensa ai dole na je yaron nan ko dan na ringa masu nasiha, wai Khausarar ce yace matarsa? Nan fa yace min na masa auren dole Ni na manta ban fada mata ba dazun na taho mu je in sanar mata yanzu" Wani irin cin birki TAUFEEK ya yi ya dawo yana nuna mata falonta ya ce" Koma, koma kin ji? Je ki cikin dakin in je in dawo , koma hajiata kar a shiga tsakanina da ke yan uba su ci galaba a kanmu, Ni fadan nan da muke yi ma gwara ki mana turare ta yiwu ba kalau ba" Hajia ta yi ram da hannunsa ta ce" Kaima ka fara tunanin ba kalau ba ko? Ku je zan zo da safe in mana turare dan gaskiya bana tunanin ko lafiya ku je, Husaini na gambo Allah ya sa a sauka a jirgi lafiya ka saka hular sanyi saboda mura ka kuma tabatar ka yi addu'a ka ji? A kuma ringa yin jijin nan dan yana maganin iska sosai" Alhusain a dole ya ringa dariya harda zama yana tsokanar Taufeek TAUFEEK ya yi murmushi ya yi gaba yana fadin" Maragaici in ka gama ka sameni " Alhusain ya daga murya yana fadin" ko Hajia bata fada ba Ni zan fada mata auren dole aka maku!" Murmushi ya yi ya karasa bangarensa, shi kuma Alhusain maimakun ya mike ya bi shi su shiga ƙafarsa ƙafarsa sai ya yi zamansa saman kujera fara wajen shukoki kasancewar akoy hasken fitila ya dannawa matarsa kira wace idan suka fara fira ya tabata ba zasu gama da wuri ba bale ta san zai taso in an jima ta kama tambayarsa me yake so me zata masa da sauransu dan ba zai shiga ƙafarsa kafar aminin nasa ba bai san me zasu tarda ba, ko ba komai gidan mutun mai aure ba'a shiga kai tsaye haka ba A lokacin da TAUFEEK ya tura falon ya shigo sai da ya dan zubawa falon ido ya lalubo wajen kunna fitila ya kunna Falon ya karewa kallo sai kuma ya dan gyada kai, lalle an taba matar gidan, watau yau fitilarma Hajia Yumna bata kunna ba bale a yi tunanin tardo kanshi ko wata tarba irin nata ( masha ALLAH, ya zamto ko yayane mace idan mijinki ya zo ya samu wani yannayin da bai saba gani ba ya gane, ama ba a hade masa tunani ba kulun gidansa a hargitse kamar juji baya gane fari bale baki, du iya shegen Yumnah mijinta ya gane yau matarsa a sama take dan takan saka kanshi ta kuma girka koda na cikinta kadai ne) Haurawa ya yi ya fada dakinsa ya shige bayi direct bayan ya ajiye karamar wayarsa, gaba daya yau bai dauki babar ba, dan kuwa koda yace masu na zai fita aiki ko kasuwa ba ya san sunna iya nemansa, Alhusain kuwa ya san ba zai shigo ba sai ya tabo shi dan haka suke yiwa junna , dabi'arsu ne, hasalima du tsakaninsu bai fi a irga ba suka shiga falon junna, sukan hadewarsu su sha firarsu ne a waje idan sun zo inda iyalansu suke basa sakin kari a yi ta zuba shirme ba kamun kan nan na wasu abokan mijin A nutse ya yi wanka sosai da sabulun wankansa na ruwa mai sanyin kanshi sannan ya fito da tawul yana jin dakin nasa wani iri dan yau bai samu turaren wuta ba, Wani yadi ya fitar mai tsari marar hayaniya ya saka a saman kannanun kayansa tamkar wanda zai fita anguwa sannan ya samu turare ya fesa sosai yadda ya saba kafin ya fito a nutse ya fara shiga dakin Yumnah da salama Bakin gadonta ya sameta rike da kofin kwalba cike da madara da nido sai dan karamin cokali tana sha Tunda ta amsa salamarsa ta kalle shi sau daya bata kuma kallonsa ba ta maida kanta cikin abinda take sha gabanta na dokawa hankalinta na neman tashi Dan murmushi ya saki ya karasa bakin gadon ya zauna ya sake dubanta a tausashe ya ce" Ina yini Yumnahna" Yumnah ta lumshe idannuwanta hawaye ya bale mata, a hankali ta fashe da kuka Ajiyar zuciya ya sauke a nutse ya janyota jikinsa ya rungumeta yana taping din bayanta kadan kadan, a hankali ya furta" Its ok Yumnah, ya isa haka kin ji?" Yumnah ta ringa sauke ajiyar zuciya tana jin yadda kirjinta ke dokawa Ya rab shin yaya zata yi da ranta? Ta yiwu a ga laifinta, tana yiwuwa a ki yi mata uzuri, sai dai ba zata iya ba kowa hakuri a kan abinda take ji ba, ita ta san ba laifi take aikatawa ba, kuma mijinta ya isa ta yi kishinsa A sanyaye sosai ta furta" yayanmu....., Na kasa hakura, yaya zan yi in iya hakura?" Sosai ya ji tausayinta ya kama shi, a tausashe ya cirota a jikinsa ya kama hannayenta yana kallonta ya ce " babu abinda zai kusanta ki da samun nutsuwar zuciya irin addu'a, sannan idan har bakya so ku zauna a waje daya kina da ikon zaba domin Musulunci ya zo mana cewa sai idan mace na so a hadata da abokiyar ZAMANTA ake haɗawa ......" Da dan sauri ta kure lebensa da kallo, lokaci daya take ta tunanin maganarsa, hakan na nufin a fida Khausar daga wannan gidan da wannan banzar kakar rasa take ita a barta daga ita sai Hajia tana hannata rawar gaban hantsi? Ba zai yiwu ba, idanma Khausar ta yi nesa kennan ba ranar rabuwa tsakaninta da mijinta? Ba zai yiwu ba! A hankali ta girgiza kanta ta ce" Ka barta a nan, kar a kaita ko'ina ta zauna a nan din" TAUFEEK ya dan zubawa yannayinta ido, sai kuma ya dan lumshe idannuwansa yana rike da hannun nata ya ce" Shikenan, ama ina so ki kwontar da hankalinki ko dan abinda yake tare da ake, idan kin ji hankalinki zai tashi kuwa ki yi ta yin addu'a in sha Allah zaki ji sauki a ranki, Yumnah ban karra aure dan bana son ki ba believe me" "Yayanmu, ka karra aure ko aka aura maka ita? Ka daina cewa ka karra, ka daina ɗorawa kanka abin nan Please" Yumnah ta fada tana sake duban fuskarsa TAUFEEK ya zuba mata ido, yannayin na so ya fara damunsa fa, gaba daya kamar wace bata gane yarensa A nutse ya saki hannunta ya mike ya karasa wajen tufafinta ya dauko mata hijab baba ya karaso ya mika mata Amsa ta yi ta saka tana jiran karin bayani dan ta san ta yiwu fita zasu yi sai ta ji ya ce" *NI NE NA KARRA AURENA, BA AUREN DOLE KO NA HADI AKA YI MIN BA, MU JE HUSAIN ZAI MAKU SALAMA*" Tamkar ya caka mata mashi ta ji a kirjinta A raunane ta bi bayansa da kallo har ya karasa ya bude zai fita ta ji karrar bude kofar dakin da take kyautata zaton na Khausar din ne, dan haka da sauri ta taho ta riko hannunsa cikin nata harda rabun masa a Jikinsa a lokacin da suke bayyana a gaban Khausar wace ta fito hannunta rike da kaskon turaran wutar da ta sakawa dakinta bayan ya kama sosai ta ji tana ra'ayin sakawa a falon sai ta zuba wadatace ta dora hijab saman doguwar rigar yadi mai santsi dake jikinta ta fito dan kaiwa falon idannuwanta suka sauka a kansu Wani irin abu ta ji ya caki makogwaronta, a hankali ta bi talabar da TAUFEEK ya yiwa Yumnah da kallo kafin ta dauke kanta tana tabe baki wanda tabe bakin tsaf a cikin idannuwansa ta juya bata ce masu ufan ba ta fara yin gaba a nutse ya sauka kasa turaran wutar nan na tashi ta karasa falon ta ajiye ta juya da nufin komawa sama TAUFEEK da ya hanna kansa Binta da kallo ta karfi da yaji cike da basarwa ya ce" Kar ki koma ki tsaya ku gaisa da Husain" Yana gama fada ya fice a falon gaba daya, ita kuma ta ja ta tsaya tana kallon kofar da ya fita kirjinta na bugawa da wani haushinsa da take ji wanda ta tabata na abinda ya mata da safe ne ba komai ba Yana fita Yumnah ta koma sama da sauri ta Kunno nata turaran itama ta sauko da shi, tana shirin ajiyewa ta dauke na Khausar din suka shigo Taufeek a gaba shi a baya bakin Husain da salama Idannuwan TAUFEEK ne suka sauka a kan kasakan turaran wutar, a ransa ya ayana'To fah' Su duka suka Amsa, Khausar ta yi kamar bata ga abinda Yumnah ta yi ba ta maida dubanta kan Husaini tan murmushi ta ce" Yau dai ga Besty, yaushe a gari?" Yumnah kuwa sai ta wuce dan kawo masa ruwa a lokacin da Husain ke fadin" Aa a yi haka? Hajia bestyn besty ai ba zaki gane Ni ba jiya kai a lulube ana kukan ba za'a zo gidanmu ba bayan mu din nan mun riga mun rike kuma sai hakuri" Da dan mamaki ta dago dan kallonsa jin bayaninsa sai ta ga TAUFEEK na kallonta, shi kuma sam bai wani tsareta da kallo ba magana dai yake yi normal , danma sun saba ne a da ya zamto a yau ya dan tsokaneta, basu taba irin haka da Yumnah ba Kasa cewa komai ta yi ta sada kai cike da jin nauyi Yumnah ta ajiye masa jus ta koma saman kujerar dake dan kusa da TAUFEEK ta zauna hankalinta a kan mijinta tana jin Husaini na mata godiya, ama kuma bai bude ba ya dai dauka ya rike a hannunsa , ita kuma a ranta tana ayana' Ni da ke a ga wanda zai fi samun shiga a fadar TAUFEEK!' (Shi fa wani son, Allah ne ke halitarsa a ran bawa, ba dan an cika kyau ko isa ko matsayi ba, a'a, wani son kai dan adam sai ka ga mema aka gani na so din ne? To halitta ce da Allah ke halitarwa ya kuma hada da wanda ya ga ya dace, Allah ka sa mu so domin ka, mu kuma ki domin ka) [7/24, 10:04 AM] +234 816 049 3429: 💔💔💔💔❤‍🩹❤‍🩹💔💔💔💔 *DA CIWO A ZUCIYATA* 💔💔💔💔❤‍🩹❤‍🩹💔💔💔💔 _MALLAKIN_ *SAJIDA NIJAR* *FREE BOOK NE* 5️⃣4️⃣ *GARABASA, GARABASA, PROMOTION, PROMOTION DIN LITATAFAN MARUBUCIYAR A KAN FARASHI MAI SAUKI 1K, YAN NIJAR KUWA 1000 FRANCS CEFA* 1: Duk karyar kada 2: Yar mahaukaciya 3: Neman na kaina 4: Bani da zabi 5: Bak'a ce 6: Kutkale 7: Makauniya ce 8: Mage 9: Duk nisan jifa 10: Idan ka raina inda kake 11: Dutse 12: Alkalamin kadarata 13: Bani da zabi 14: Dakika Biyar 15:Wata kokowar 16: Aure yakin mata 17: Ni zan ladabi 18: Daga tafia daukar soja *Dukansu a kan farashi mai sauki, zaka saka dubu guda ne domin promotion ne nake yi, ka tuntubeni kan layina kamar haka +227 93 81 16 18, Sajida Nijar* Now *Da CIWO A ZUCIYATA* *Tallah, tallah, tallah* *SECRET DE LA FEMME DU MANGA* _Gidan Kamshi, Sirrin Manyan Mata, nesa tazo kusa,Amarya ,Uwar gida,Ango da mai gida Har ma da yan mata da samari shin kuna sane da cewa HAJIYA FUSAM ta shirya tsaf domin gwangwaje ku da turarakunta masu dankaran kamshi? Tare Kayan gyaram jiki na musamman ,wanda daga nesa kamshin ki kadai ya wadatar ya isar da sakon zuwanki waje,gidan ki kuwa sai ya zam abun kwatance wajen kamshi, kar na cika ku da surutu bara in fara zayyano su_ Farar Humura Bakar Humura Humura special, humura de bain Humura epicé Lait de nuit Parfums désodorisant Parfums rideau et dras Lait de nuit Alkam Kulakcam *Waɗannan kadan ne daga bangaren turaran ruwa* Gagab, sandal flex, Durot, durus, sandal fleur, tafarce, farce, sandal bangui, sandal, hypotonic sandal, al'ut, coktail creation VIP, Gajiji, Mankaji, turaran wutar labule da cafet, Aba malan, boulettes *Munada bangaren gyaran jiki kamar haka:* mai mai saka santsin jiki, mai mai kanshi, Kayan gyaran jiki mai saka fata ta yi santsi da laushi, kayan gyaran jiki mai saka fata ta yi fari, Sabulu mai saka fata ta yi haske, sabulu mai saka fata ta yi santsi, sabulu mai goge yanayin fata, mai wanda baya saka fari mai gyara fata Sayen na gari mai da kudi gida,sai an gwada akan san na kwarai💃💃 Hajiya Fusam na zaune a kasar Niger domin yin magana da ita kai tsaye tuntuɓi wannan number 97 82 44 94 *SECRET DE LA FEMME DU MANGA* Gidan Kamshi, Sirrin Manyan Mata💃💃💃💃💃 A sanyaye Mama ta ce" Ka san yanzun ko babu abinda ya daga mata hankali abin na tashi, dan dai bai kai na yau ba dan idan ya tashi da na bata maganinta ta samu barci yake wucewa shi yasa baka Sannin ya tashinma" Hajia Nawarah dake zaune a ranta gani take yi harda rashin godiyar Allah a wajen mijin nata da matarsa da kuma dansa, , ita dai bata jima sosai tare da su ba ama ko ita ta san cewa zuwa yanzu ai shekarun Hajia sun kai wajen ciwace ciwace irin na girma masu zafin nan da ace bata samun kulawama da tuni ta kwonce ai, dan dai ga kulawa, ko abincinta ba irin na kowa bane, jikanta ya dora doka ko tuwon laushi za'a tuka mata da irin abincin masu diabete ake yi mata, sigan bangarenta na masu diabete ne, kai komai da ka sani yana taka tsantsan da shi yana kuma hankalce da shi baya yarda ko da wasa ta yi wasa da lafiyarta, sannan a dole ta saba da sport rawata kaffafuwanta dan a lokacin da ya ga ya dace ya sakata tafiyar shine ke fitar da ita cikin anguwa da duku duku sunna tafe sunna fada har Mai kwanoni shima yake binsu dan wani lokaci har dariya suka bata ita kam a ranta ta ayana' Rai dai ana sonka sai an rabu da kai, du abinku Hajia ai yanzun tana hararan kabari, du kaunar ku da ita kuwa ba zaku hanna ba' Hajia dake sauraron zancen itama ta budi baki a matsayinta Na matar gida dadadiyar da ta rigayi kowace ta ce" To Elhaji ciwon zamani sai an tankwaloshi, ana gudunsa yana bin mutun bale masu ciwon hawan jinnin nan an ce ba'a cika so sunna yawan fada ba, Allah dai ya ba Hajia lafiya baiwar Allah du ta yi wani iri" Elhaji ya amsa da amen, ya maida dubansa kan TAUFEEK wanda bai furta masu koda A bane Jim kadan nurse da ta je da kayan aune aunen jinnin Hajiar ta dawo da result Bata tsaya ba ta shige ta kaiwa doctors da Khausar dake zaune daf da gadon Hajiar tana rike da hannunta daya tana tofa mata addu'a dayan kuwa yana ɗauke da karin ruwan da doctors ya jona mata Sunna gama gannin komai Doctor ya umarce su kan sunna iya tafia Ya zamto shine karshen fitowa sai Khausar dake bayansa rike da wasu takardun da ya bata da kansa haka kuma kaf likitocin sun yi mamakin gaannin Khausar din da Hajia dan babu wanda ya san matarsa take haka kuma basu san ko members din family din Professeur din bace Su Baba ya fara tsayawa ya kwontawa da hankalin cewa ta samu barci da sauki kamar yadda likitoci ke sanarwa wa'inda ba likitoci ba Sannan ya dawo wajen da TAUFEEK ke tsaye daf da Mama ya amshi result din Hajiar ya mika masa sai ya dora da fadin" BP dinta ya yi kasa sosai ne, haka kuma sigan jikinta ya yi kasa fiye da misalin mai cuta irin nata, ga kuma ciwon kan da zazabi, mun saka mata maganinta na da wanda ya shafi siga din, ama na hawan jinnin na saka mata sabon treatement dan wancen din inaga ya fara sakin jikinta ne , zazzabin kuwa na saka karin ruwa da allurar saukar da ciwon kai da kuma na zazzabin wace zamu ringa saka mata du tsakanin awa shida, sai dan tari wanda in sha Allah shima zamu saka nasa maganin idan wannan ya daidaita, yanzu zamu ajiye nurse din da zata zauna kusa da ita dole wace zata ringa kula da hawan jinnin nata kowani lokaci har mu ga yannayin saukarsa, in sha Allah zata samu lafiya Sir " Taufeek ya hadiyi dan yawun dake tsakanin harshensa da makogwaronsa , a hankali ya ce" Zan zauna da ita Doctor" Doctor ya dan dube shi, dama ya san yakan iya cewa shi zai zauna da ita ama kuma nurse din da za'a saka ta zauna kusa da Itan anya zata iya aaikinta yada ya dace kuwa? Dan idan yana waje sukan rikice ne wani lokacin idan ana gudun kar a yi laifin nan ake aikata laifin ba'a sani ba, dan haka sai ya ce" I'm sorry prof da ka yi zamanka a office idan ya so sai komai ya ringa samunka a cen ko kuma ka ringa saukowa kana komawa dan likitar ta samu filin yin aikinta a nutse" Khausar dake tsaye dan nesa da su rike da takardun ta budi baki a sanyaye duda ta san ba itace da ɗaukan wannan decision din ba , ama sai ta kasa hanna kanta fadin" Doctor, Please zan zauna matsayin nurse din tare da prof in sha Allah " Doctor ya dan kalleta da mamakin yadda ta iya fadin haka a gaban TAUFEEK kanta tsaye Tashi daya ya nuna ba zata yi ba dan ba ita ta saba kulawa da ita ba Shi da kansa likitan ya fadi haka ne dan baya so ta jawa kanta fada, dan likitocin ba sunne suke da ikon yin hakan ba, uwa uba Khausar ba likitar jinya bace takardarta ya wuce nan A hankali Taufeek ya dakata daga nufin nufar wajen Baba ya juyo a dakensa ya ce" zata iya zaman , *SHE IS MY WIFE*" Daga nan ya karasa yana fadawa Baba cewar su je gida kawai shi yana nan , kuma sun san harkar asibitinsa ba'a zama a yi jinya, shi dai zai zauna Khausar kuwa zata yi jinyar, dan ya hada kan matansa su juya baya son rigima da hayaniya a kai Likitan kuwa sosai ya yi mamakin jin Khausar matar Doctor ce, sai dai bai tsaya ya wani nuna mamakin nasa a fili ba ya yi gaba yana fadin " Madame bismillah mu je na baki dukkan abubuwan da ake mata da takardar " Khausar kam tunda ya fadi cewa ita matarsa ce sai ta ji dama ba a gaban Doctor din ba tace zata zauna, sai ta ji kunya da nauyin su Mama da suka ji maganar, ta bi likita shina cike da jin nauyisa ta je ta amso magungunan Ko da ta dawo ba kowa ta shige dakin ta kai komai ta ajiye ta juyo inda yake zaune rike da hannun Hajia yana kallonta A nutse ta dauko kujera ta ajiye daf da shi a hankali ta samu kanta da dora hannunta saman nasu a hankali ta dan matsa nasan kadan sannan ya dan bubuga a hankali ta ce" in sha Allah, zata samu sauki, ka kwontar da hankalinka Please" TAUFEEK ya juyo yana kallon fuskarta, a hankali ya dago hannunta ya kai gefen fuskar tasa ya shafa gefen fuskar nasa da hannunta na dama yana kallonta kasa kasa ya ce" Allah ya sa " Daga nan Khausar ta yi shiru suka ci gaba da kula da Hajia da dukkan motsinta Sosai take barci mai daɗin gaske, sunna nan direba ya kawo suturar TAUFEEK wanda ya yi kira ya saka Yumnah ta dauko masa sannan ya fada mata ba sai ta zo ba dan ba barin jinya ake yi ba domin ta nuna tana son ta zo din itama ( wani lokacin, idan da rabo , mai hali irin na Yumnah na cenzawa idan ya samu abokin kwaikwayar halayar nasa mutun ne mai aikata aikinsa domin Allah ba dan a yabe shi ba ko dan ya saka dan uwan nasa jin haushi da kishinsa ba.) Office dinsa ya je ya yi wanka ya cenza sannan ya shigo masu da abinci Sallah kadai ke fidashi, Khausar kuwa tunda ta shige bata fito ba dan idan bayin ne akoy komai a ciki, kawai dai kayan jikinta take jin sun kai cenzawa dan kuwa ita rage acn nan ta yi sosai ta kuma kashe panka dan TAUFEEK har fifitu yake yi wai zafi ita kuma ta nuna tarin da Hajia ta fara in ta farka cikin sanyin nan da mura zata tashi, A haka har aka fito daga sallar isha i, zuwa lokacin sosai jinnin Hajiya ya daidaita sai dai kasancewar bata farka daga barcin da take sha ba ba za'a iya tantance irin aikin da magungunan suka yi mata ba, ama ko a yannayin saukar numfashinta da sauki sosai A hankali ya mike daga daf da Hajiar ya zubawa bayi ido Kasa hanna kansa shiga ya yi a hankali ya bude ya shiga yana wani irin fatan da bai dace ya yishi ba a zuciyarsa a matsayinsa na abokin Khausarar Aba Allah ya taimaketa tana tsaye tana alwallah ne, sai dai duda haka ta wanke pant dinta kennan ta shanya bayan ta yi wanka sama sama sannan ta yi bruch ta maida rigar da take yin datinta yanzun sosai a ranta guda ba wani dati da ta yi ta shiga yin alwallah hankali kwonce dan tunda take nan ta ga babu wanda ya shigo bale a ga paant dinta Da sauri ta kai dubanta inda ya zubawa ido, a rikice ta kwalalo ido ta budi baki zata yi magana ya tako da saurin da bata yi zato ba ya janyota jikinsa lokaci daya ya dago kanta ya hade bakinsa da nata ya shiga kising cikin saurin da ya saka ta jan numfashinsa ta hadiye a huhunta sannan ya sake juyawa da ita ya hadeta jikin bangon nan a hankali hannunsa na damkar cinyarta ya ki bata damar kwace bakinta sai da ya gaji dan kansa sannan ya saketa yana fitar da numfashi da sauri da sauri ya janyota jikinsa ya sake rungumeta tsam har sai da ta kwontar da kanta dan dole a kirjin nasa tana sauke numfashi A hankali ya dan yi kasa da bakinsa daf da kunnenta Cikin kwarewa a aikinsa ya ringa sinsinar kunnen nata yana dan sauke hucin numfashinsa a nan, kasa kasa sosai ya ce" Ba'a magana a bayi, kin ga kin saka na maki abin nan da bakya so ko?" Khausar ta dago da sauri ta zubawa fuskarsa ido, a rashin shiri ta ce" Kai TAUFEEK walahi da gangan ne ba gashi ba ka yi maganar ba?" TAUFEEK ya dan zarro idannuwansa da hannunsa ya mata alamun ta yi shiru mana kafin ya nuna mata pampon wai ta yi abinda ya dameta tana yi Ajiyar zuciya ta sauke ta koma ta bude ruwan ta daura alwallar tana kiyayewa kallonsa dan gudun kunyar dake nukurkusarta ta kayar da ita har ta gama cikin dabara ta janye pant dinta ta dauki hijab dinta ta nade shi a ciki da nufin in ta faki idonsa zata maido ta shanya ta yi gaba sai turo baki take yi ta bude bayin ta fito shi kuma yana baya yana kwasar ganima wa idannuwansa yana kashe kwarlwatar idonsa Idannuwanta ta mutsitsika tana sake dubansa daga zaunen da ta kama ta zaunar da kanta da kanta ta sake rage girman idannuwanta tana dake tabatarwa kanta abinda take gani ta dauke kai ta ce" Uhum ikon Allah, dubun munafukai dai ta cika, dama karya fure take bata ya'ya, to Ni du wanda ya kuma min iskancin kukan baya son auren nan sai dai mu daku da ubansa koma waye, aikin banza a asibitin zaku shige bayi to uban mema kuka yi?" Sai da cikin Khausar ya motsa, a rikice ta kalli magidanci wanda farin cikin gannin Hajiar zaune ya kasa barin fuskarsa da sauri ya zagayo Khausar ya karasa yana fadin" Yaushe kika tashi tawan?" Hajia ta sakar masa harara tana leken Khausar ta ce" dole ai ka tambaya tunda kun sumar da Ni kun shige kun aikata aikin da ba shikenan ba, Allah dai ya sa ba a bayi zaka min jika ba kai marar hakurin tsiya, dilla dubaka kamar ba kaine ke min rashin daga a kan auren nan ba, to da mai kwanoni kake, sai ku kuncen abin nan mu je gida ka samu filin baje kolinka a mutunce kar ka haifon dan bayi ya ringa kantara min mari, ke kuwa kya karaso ko sai na taso na tardo ki, ashe haka halinki Khausara? Baki kamar agwaluma kina ihun bakya son auren magidanci shine zaku munafunceni a bayi bayan kun sumar da Ni?" A rikice Khausar ta rarumi hijabinta gaba daya ta manta da pant din ta zurma hijab din ta karaso tana yadda hannayenta ta ce" Hajia, walahi walahi ba abinda kike zato bane, hasalima babu abinda ya hadani da shi gayanan ki tambayeshi Hajia" TAUFEEK ya tabe baki yana mikewa ya ce" ai kuma sai ku yi" hankali kwonce ya karasa ya dauki pant din ya shiga ya shanya ya dawo ya zauna yana kada kafa Hajia na mitar su je gida ya dubeta ya ce" Ke kam wai wace irin mutum ce, kin farka zaki dagan hankali kuma ko? Babu inda zamu je sai kin warke sumul , kuma maganar tafia babu ita, dan babu inda zamu je kina rashin lafiya " Hajia ta yi tsuru tsuru tana kallonsa, sai kuma ta kalli Khausar ta ce" Khausara kin gama sallar ne?" Khausar ta juyo tana gyada kai Hajia ta ce" Je aro mana waya ki amshi numbar mai kwanoni a wajen wancen mu buga masa waya kin ji? Ba da Ni ba wannan rashin kunyar tana tafe kana lekenta kuma bayan wannan Madina ai Garin Manzo in Allah ya taimakeni kasata a cen shikenan sai ka ki kaini dan son kai? Ni sai mun je bana " A hankali suka zuba mata shi da Khausar din A sanyaye ya tashi ya karasa bakin gadon ya zauna daf da ita ya kamo hannayenta yana dubanta ya ce" Dan kina son tafia gida ne zaki daga min hankali ko?" Hajia ta sauke ajiyar zuciya, sosai jikan nata ke bata tausayi idan ta masa maganar mutuwarta ko me suke yi sai ya sakar, nan da nan ka ga ya zama wani iri, tamkar yaro karami ko kuma tamkar ba likita ba Cike da rashin kwarin gwuiwa ta ce" Ni mu koma gida" Ajiyar zuciya ya sauke ya ce" Ok ina zuwa" Daga haka ya fice dan daidaita tafiyar tasu dan ba zai iya yana kallonta a haka ba, tunda gidan take so za'a tafin mata da komai da komanta a ringa mata treatement din a gida Yana fita Hajia ta share hawayenta a boye ta kalli Khausar dake ninke kayansa tana hada yan tarkacensu ta ce" Kin ga mijinki ko? Baya so a raba min mutuwa, bayan ya san cewa aya ce, lokaci kawai take jira ta dauka, ta dauki jaririma bale Ni? Ama a kulun idan na kalle shi nakan ji tsoron ranar da za'a sanar masa bana cikin rayayyu, sai dai da Ni da shi da kowama duka lokaci muke jira, Khausar dan Allah ki so TAUFEEK, ya rayu da son ki, ban san me zan ce maki ba, abinda na sani shine abotarku ke kika dauketa abota, shi a soyaya ya dauketa, mai zafin da baya jure ganninki da kowa, ki masa uzuri na nauyin baki da jinkirin sanar maki, kin san kowani dan adam da irin yadda Allah ya halice shi, kar hakan ya sa ki kasa bashi kulawar da ta dace, idan har kika yarda kika aminta da mijinki bayan amininki tabas zai zamto du wani nau'i na farin cikin gidan duniyar da kike iya daga hannu ki roka wajen Allah, ban ziga shi ba , ban kuma kuranta shi ba, haka kuma ban ce maki bashi da Laifuka ba, ta yiwuma ba irin namijin da kike yake ba a duniya, sai dai ina mai rokar alfarmar dan Allah ki bashi dama, in sha Allah zaki ji dadin zama da shi, sannan kar ki zubar da tarbiyyar ki, ki sani itace abu mafi daraja a tare da ke, ki girmama du wani wanda ya girmamaki, zaki ga kamar na takurawa matarsa, sarai na san abinda nake yi, dan Ni san abinda na gani tare da ita, ina mata haka ne dan ta ankara ta gane domin babu mai kwabarta ta wannan sigar, gaba dayanku ina sonku daidai misali da ace yau zan wayi gari in ga da'a a lamuranta da sai ta ji dadin zama da Ni, ama ina mata adu'ar samun cenzawar halaya daga Wadinnan zuwa na alkhairi, ki yi kokarin yin hakuri da halinta kin ji?" Khausar da kanta ke sade a sanyaye ta ce" In sha Allah Hajia zan kiyaye" Sai dai a zuciyarta sosai zuciyarta ke cike da tambayoyin da ta san ba zata samu amsarsu da sauki ba, abinda ta sani shine kalmar nan ta shige ta fiye da komai kuma ta mata fashin bakin da bata jin haushinta a ranta, ama kuma bata san a yaya ta dauketa ba Sunna yar firarsu ya dawo Shine ya cire nata karin ruwan ta mike da kafarta tana tafia a hankali sunna biye da ita har suka je mota ya taimaka mata ta shiga sannan ya ja su suka nufi gida sunna tafe sunna fira da rikici kamar ba ita ke rashin lafiya ba Sunna isowa sai da ya maida mata karin ruwan ta ya gama shiga sannan ya tafi bayan ya yiwa Mama salama wace ta zo bangaren Hajiar da nufin zama har Hajiar ta murmure Sai bayan ya tafi da kamar wasu mintina Mama dake zaune Khausar na murza mata man zafi a kafafuwanta ta dago jin Hajia na gyaran murya tana sauraron Hajiar da ta fara magana tana fadin" Ni Dije na ga abu, wai ba zaki salameta ba ta tarda magidanci? Ina kara sai kin sa na tofa gaskiya ke dai Allah shirye ki, sabon aure ne fa kuma fa na kiya muka dawo ai dan na kula da cutuwa ke sai ki wani riketa?" Mama ta dan zarro ido tana duban Khausar ta ce" Lah, tashi ki tafi Khausar tashi" Khausar kam sai ta koma irin Yaren TAUFEEK, ta zubawa Hajia ido tana tunanin yaya zata yi da bakin Hajia? Har sai da Maman ta sake korarta sannan ta mike jiki ba karfi cike da kunya ta gudu A lokacin da ta bude Falo Yumnah na zaune tana game da wayarta sabuwa Salama ta yi mata da kula , ba tare da jiran ta gaisheta ba ta ce" Barka da warhaka Yumnah, yaya gida?" Yumnah ta dan dakatar da abinda take yi ta zubawa Khausar din ido na dan lokaci, sai kuma ta tabe baki tana hanna kanta yayaba mata magana dan a gaskiya ta daku fa shekaran jiya ba zata so a mata irin marin ba, karshema sai ta mike ta haura sama tana harare harare Ita dai bata ce komai ba bayan ta duba abincin ta ga babu wanda ya mata dan wasu irin girki na yan gayu ne sai ta haura sama ta je ta shige bayi ta shiga wanka Tsaf ta saka kayan barcinta mararsa nauyi ta dawo saman gadonta ta cenza abin gadon sannan ta haye tana adu'ar barci ta lumshe idannuwanta ta rungume jikinta ta shiga neman barcin dan a gajiya take sosai Har sai da sha biyu ta gora ta ringa jin ana tashinta A hankali ta bude idannuwanta ta sauke a fuskar TAUFEEK dake zaune daf da ita sosai A hankali ya ce" Tashi in baki abinci ki ci" Khausar ta bi plate din dake hannunsa da kallo, a hankali ta yi dan luuuu da idannuwanta tana maida su dan barcin dake cikinsu murya a shake ta ce" Bana jin yinwa Taufeek" Hannunta ya sake rikowa yana kallonta da kallon da idan da ace idannuwanta biyu da sai ta tsorata, muryarsa a shake ainun ya ce" Ki yi kokari ki ci ko yayane dan kar ki wahala..........." Sam bata gane yarensa ba ta komawarta tana lulubewa cikin abin rufar nan Ajiyar zuciya ya sauke a nutse ya maida plate din sannan ya dawo ya haura gadon bayan ya kashe duka fitilun dakin A hankali ya shiga janye abin rufar nata, ita kuma ta kasa rikewa saboda barcin da ya ci karfinta Cikin nutsuwa ya dora hannunsa saman cinyoyinta a hankali ya shiga shafawa har ya kai daidai wajen bude rigar sannan ya bude cikin nutsuwa ya kama rigar ya ringa saukota daga jikin.......😨😨😨😨😨💃🏻💃🏻😨😨😨😨😏💃🏻💃🏻 Mun shiga uku🥹 😂💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻😂😂😂😂😂 [7/29, 9:22 PM] +234 806 191 8478: 💔💔💔💔❤‍🩹❤‍🩹💔💔💔💔 *DA CIWO A ZUCIYATA* 💔💔💔💔❤‍🩹❤‍🩹💔💔💔💔 _MALLAKIN_ *SAJIDA NIJAR* *FREE BOOK NE* 5️⃣5️⃣ *GARABASA, GARABASA, PROMOTION, PROMOTION DIN LITATAFAN MARUBUCIYAR A KAN FARASHI MAI SAUKI 1K, YAN NIJAR KUWA 1000 FRANCS CEFA* 1: Duk karyar kada 2: Yar mahaukaciya 3: Neman na kaina 4: Bani da zabi 5: Bak'a ce 6: Kutkale 7: Makauniya ce 8: Mage 9: Duk nisan jifa 10: Idan ka raina inda kake 11: Dutse 12: Alkalamin kadarata 13: Bani da zabi 14: Dakika Biyar 15:Wata kokowar 16: Aure yakin mata 17: Ni zan ladabi 18: Daga tafia daukar soja *Dukansu a kan farashi mai sauki, zaka saka dubu guda ne domin promotion ne nake yi, ka tuntubeni kan layina kamar haka +227 93 81 16 18, Sajida Nijar* Now *Da CIWO A ZUCIYATA* *Tallah, tallah, tallah* *SECRET DE LA FEMME DU MANGA* _Gidan Kamshi, Sirrin Manyan Mata, nesa tazo kusa,Amarya ,Uwar gida,Ango da mai gida Har ma da yan mata da samari shin kuna sane da cewa HAJIYA FUSAM ta shirya tsaf domin gwangwaje ku da turarakunta masu dankaran kamshi? Tare Kayan gyaram jiki na musamman ,wanda daga nesa kamshin ki kadai ya wadatar ya isar da sakon zuwanki waje,gidan ki kuwa sai ya zam abun kwatance wajen kamshi, kar na cika ku da surutu bara in fara zayyano su_ Farar Humura Bakar Humura Humura special, humura de bain Humura epicé Lait de nuit Parfums désodorisant Parfums rideau et dras Lait de nuit Alkam Kulakcam *Waɗannan kadan ne daga bangaren turaran ruwa* Gagab, sandal flex, Durot, durus, sandal fleur, tafarce, farce, sandal bangui, sandal, hypotonic sandal, al'ut, coktail creation VIP, Gajiji, Mankaji, turaran wutar labule da cafet, Aba malan, boulettes *Munada bangaren gyaran jiki kamar haka:* mai mai saka santsin jiki, mai mai kanshi, Kayan gyaran jiki mai saka fata ta yi santsi da laushi, kayan gyaran jiki mai saka fata ta yi fari, Sabulu mai saka fata ta yi haske, sabulu mai saka fata ta yi santsi, sabulu mai goge yanayin fata, mai wanda baya saka fari mai gyara fata Sayen na gari mai da kudi gida,sai an gwada akan san na kwarai💃💃 Hajiya Fusam na zaune a kasar Niger domin yin magana da ita kai tsaye tuntuɓi wannan number 97 82 44 94 *SECRET DE LA FEMME DU MANGA* Gidan Kamshi, Sirrin Manyan Mata💃💃💃💃💃 Tallah 3 Hajiata, ke kin san rayuwar aure sai da anini, in babu jagab a babar eriya oga ya kama tofa yawu da neman yadda zai yi bawan Allah, idan kuma babar haja a bude ham ai ba labari oga sai dai ya shiga ya fito kamar ya shiga kofar ruwa😔, zo ki ji, a farashi mai rahusa zaki gwangwaje ki rike bakin Elhaji gudun tada yara, ama idan lamari ya yi lamari tsaf zaku karya gado☹️🫣 🔥💥🔥💥🔥💥🔥💥🔥💥🔥💥🔥💥 *HOHOHO WANI KAYA SAI AMALE, DON JAKI BAZAI 'DAUKA BA, INA MATA MASU BUK'ATAR 'DAGA DARAJARSU A WAJAN MAZAJENSU INA MATAN DAKE SHAN WULAK'ANCIN MIJI KO NA KISHIYA ,INA MATAN DAKESON ZAMOWA MOWA AGIDAJEN AURENSU TO ALBISHINRU MAMAN ZARAH YAR MUTAN SOKOTO TA SHIRYA TSAF DOMIN GABATAR MAKU DA ZAFAFAN KAYAN MATA MASU KYAU DA INGANCI WANDA BASUDA ALGUS ACIKI , AKWAI MAGANI DANAYI BINCIKE AKANSU DAN FARIN CIKIN MA'AURATA NAMU BA IRIN NASU BANE KAYAN MU NA DABAN NE NA ASALIN SAKKWATAWAN SHEHU MASU ABUN MAMAKI* 07034251528 kayanmu masu inganci ne masu ladaftar da kowane irin namiji Kad'an daga cikin abubuwan da muke dasu Ingantaccen maganin nono , Wanda zai gyara maki nononki donmin dawo da martaban nononki acikin kankanin lokaci komai lalacewarshi kuwa sauran bayani sai mun had'u pc +234 703 425 1528 Maganin hips (hips up) Wanda zai ciko maki da hips dinki su cika suyi bul bul ga laushi dasu k'ara suyi dass abun sha'awar kowane namiji Maganin infection Sha yanzu magani yanzu Yana fatattakar sanyi cikin kankanin lokaci magani ne na maza da Mata insha Allah kowane irin sanyi gareki kikayi amfani dasu anwuce wajan Ingantacce Kuma sahihin maganin k'iba Wanda Zaki ciko acik kankanin lokaci zakiyi kibar ki Yar dai dai misali ki huta Zama da Rama Baki rasa ci ba Baki rasa sha ba amma kullum Ana kallon cewa kinada matsala agidan aurenki saboda wannan ramar , Rama batayi ba Sam Yar uwa Sabulun wanka Kalolin sabulun tsarki Turaren tsugunno Turaren al'ajab Hatsabibin turare Da sauransu 07034251528 Kalolin gumba Gumbar Dabino Gumbar gero Gumbar madara Gumbar matsi Gumbar ukku bala'i Gumbar tada zaune tsaye Gumbar sabon budurci Gumbar sa buzu kuwa Gumbar aya da kwakwa Gumbar ridi Gumbar mazari Sarauniyar gumba 3in1 Da sauran kalolin da bansamu fadi ba, Kalolin gari Garin mallaka Garin hutar da malaminki dakan jaraba Dakan Amare Dakan Ni'ima Dakan kishiya in bakiyi bani waje Garin sa buzu kuwa Garin buje.sharkaf Garin Dan la'asar Yayan hadiya mai suna dan la'asar Original Dan goshi Original Dan goshi (sabon salo) Original man damo Original man ayu Kitsen damo Sirrin tafin kafa Sirrin farinjini na uwargida da amarya harma da yan mata Kwallin idonka idona Muna hada set na sirrin mallaka hajiya ba boka ba Mallam sai tarin sirrika kema kizama kowa agidan surenki Akwai hadin sabon budurci ga yarinyar data rasa budurcinta ta hanyar fyade ko yaudarar d'a namiji da izinin Allah akayi maki wannan hadin to an wuce wajan sauaran bayani sai mun had'u pc Kalolin tsumi Tsumin mallaka Tsumin jaraba Tsumin madarar ni'ima Tsumin tabaje Tsumin Amare Tsumin sabon budurci Tsumin nono rakumi Matan gaske Ruwan jaraba, Da sauran kalolin da ban fada ba Kalolin matsi da basuda illa ajikin mace sai dai ma sukara maki lafiyar Matsin Dan mannau Matsin mallaka Dan la'asar Sabon budurci Mak'alemata Mashahurin matsi Ukku bala'i Matsin uban budurwa Akwai gumba ta matsi wadda Shanta akeyi ga matan da basa son yin matsi Muna hada set ga wadda Allah ya jaranfa da matsalar fyade har yarasa budurcinta , muna hada mata kaya ingantattun don dawo da martabar ta, Hohohohoho in ana dara fidda uwa ake *Kyallen al'ajabi* babban sirrin mallaka mai abun al'ajabi mallaki naki don samun damar shiga cikin jerin mata masu fada aji a gidan mazajensu , KARKU manta da sunan maman zarah sokoto sayen nagari maida kudi gida 07034251528 ina maraba daku sayen daya ko sari ina Sokoto sannan ina aikawa kowane gari cikin aminci da yardar Allah Ga Wanda suke bukatar ganin kalolin kayana to suyi sarving number na suyimun magana nayi sarving number ku zaku dinga ganin kalolin kayana a status ngd sosai 07034251528 Maman zarah mabera SOKOTO A hankali yake sauke rigar, wace ta kasance mai mabalai ne kawai, kuma sabuwar rayuwar da yar gidan Aba ta ara ko ta rike a matsayin wace take yi a da ama da katon hijab dinta a da din, yanzu kuwa babu shi, sai ya zamana yana bude rigar a hankali yannayin hucin jikinta ya tabatar masa cewar bata tare da komai daga ita sai rigar ne Wata irin ajiyar zuciya ya sauke gannin ta fara motsi mai nuna alamun zafa ga farka Bai hannata ba har sai da ta bude idon da sauri dan jin sanyin dake ratsata ya wuce misali, dan idan baka da komai da idan da sutura komai kankantarta da bambanci a yannayin jin sanyin mutun A birkice ta rike hannun da take ji daf da cinyarta, duhun dakin ya saka bata gane ko waye ba, bata gani Bama zata iya tsayawa ganewar ko tunanin waye zai iya aikata haka ba, a rikice ta so mirginawa tana ambaton sunnan Allah, sai dai ta ji ta kasa juyawar saboda hayowa da ya yi ya saka hannunsa daya ya riketa da hannun nasa riko mai kyau din da ya sakata sauke wata wahalaliyar ajiyar zuciya tana fadin" Muhammadu rasululahi" A hankali ya furta" Sallalahu alaihi Wa Salam" "Kamar TAUFEEK?" Ta fada a sanyaye tana sakin hawayenta Murmushi ya saki, kasancewar ya jima shi a cikin duhun yana iya gannin wasu yan motsinta, a hankali ya furta" akoy wanda zai yi min gigin zuwa inda kike ne koda ba'a halarta min ke ba bale yanzu da kike *TAWA?*" ya ilahi sosai maganar maganar ke daf da hautsina ya'yan hanjinta, a hankali ta riko hannunta da ta ji yana shafa kafarta da ita ta rike kam murya ciki ciki ta ce" TAUFEEK, Ni ce fa kawarka, kuma inaga kamar bani da sutura, dan fita in saka sutura ka ji ? Sai ka dawo in ji me kake so a dakina yauma kuma" Wayarsa dake cen ajiye ya saka ƙafarsa ya laluba ya dauko ya kunna fitilarta ba wata wata ya haske Khausar da ita Wani irin ihu ta saka tana son mirginawa ama ya hanna hakan ta hanyar gaje mata wajen sosai kuma rigar gefen hagunta a bude har mamanta ya zamto dai du rigar ta sauka a jikinta A hankali yana kallon jikin nata kasa kasa sosai ya ce" Ni ne na bude rigar" Ji ta yi tana daf da sumewa dan tashin hankali Bai barta ta idasa tunanin ko ya tako dan aljani yana son rikita masa tunani ba ya ce" inada wajen kwonciya sama da inda kike ne? Ko kina tunanin inada wajen da zan huta sama da jikinki?, Hey a nan nan ne wajen da zan ringa ajiyar yayana, nan kuma nan zan ringa saka bakina ina tsotsa har safiya ta waye" ya karashe yana nuna mararta da kuma mamanta A yanzu yar gidan Aba idan bata suma ba gaskiya tana da kokari sosai Domin idonta idon magidanci ya ajiye wayar nan ta haske dakin baki daya, cikin ikon mai sama ya janye abin rufar gadon tas ya wurgar sannan ya mike a gaban baiwar Allah salihar baiwa ya shiga cire nasa tufafin A rikice ta yi ruf da ciki tana fashewa da kuka, ta kuma juya ta dukunkune jikinta tana fadin" Na mutu na lalace yau me yake damunka ne?" Murmushi ya kuma yi, har cikin ransa yake tanadin wannan ranar da alkawarin ajiye komai a tarihi dan watarana ya maimaita mata A hankali ya hau gadon da dan dogon wandonsa ya kwonta a bayanta ya saka hannayensa ta cikin rigarta a hankali ya kai bakinsa daf da kunnanta ya ce" kin fa san ina son ki, kin fi kowa sani tunda ke ba makauniya bace ba kuma kurma ba, kin san nine ke fadin ba abota tsakanin mace da namiji, na sha fadi cikin firarmu, to mu ba mace da namiji bane ko dai dan daudu kike kallona? Ni kato ne Khausar kuma ina like da abinda nake so ne, kowama ya gane banda ke, kin tsaya kina bani wahala harda summa fa na yi da kika tabatar min zaki auri dan yawan taburada, wai me zan gaza baki ne? Ko kina tunanin ba zan iya da ke bane? , Ina tsoron tabaryar ta fi karfin turmin Khausar, ko zaki ce min a matsayinki na likita baki gane cewa ciwon mararki na bukatar wannan ne?, Hey ko zaki ce min bakya jin kamar ki ji ki a irin wannan yannayin bayan kin kai jin?" A rikice Khausar ta rike hannunsa ta juyo tana kallon fuskarsa hadi da sajensa har zuwa hannunsa da ta rike, tana dago fuskarta zata kuma yin magana TAUFEEK ya hade bakinsa da nata A raunane take kallon fuskarsa kirjinta na dokawa tamkar zai balo ya fito ta bakinta A nutse ya ringa ribantar dukkan wani gaba na jikinta Tun tana rike shi har jikinta ya yi mata wani irin nauyi sannan ta ji tana zubar da ruwan da ta san cewa na ni'ima ne domin ita din likita ce Nauyi da kunya da tunanin eh lalle ya san me ya fada , kuma idan ya kai wannan waje ta gama kwasar kunya wace bata tunanin ko zata iya mantawa ba ya saka ta sake rintse idannuwa tana jin irin yadda yake haukata mata ilahirin jikinta Maganarsa gaskiya ce a irin wannan lokaci da shekarunta da lafiyarta ta jima da wuce fannin bukatar jin hakan a jikinta Yana kuma da gaskiya tabata nan da yake yi ya wanzar da wani baban lamari a jikinta A hankali ya dago ya zuba idannuwansa cikin nata bayan ya yi dabara ta bude idannuwan nata A hankali ya sake dubanta muryarsa a kurya sosai ya furta" I love You so much" A hankali Khausar ta lumshe idannuwanta wasu hawaye Masu tsada suka shiga bin gefe da gefen idannuwanta Idannuwan nata ta sake lumshewa a lokacin da ya tabatar mata yana daf da kasancewa ita, ta zamto shi ta hanyar karantar adu'ar saduwa da iyali Dukan abinda yake gabatarwa cike da tausayi ne da so, da bi a laluma da kuma kulawa da lamarin lafiyar jikinta, ama du da a haka a lokacin da ya ainahin zamo dayan da ita lisafinsa sai ya kunce A lokacin da take tunanin zafin ciwon azabar da take ji ya ragu dan ya samu ya shiga hajar da yake ta kokowar sai ya shiga sai ta ji wani fitinanen tashin hankalin dan bai yi mata da wasa ba, tun tana tunanin zai daga mata kafa har ta fara kukan a bayane mai haɗe da magiya da neman kubutar rai Sai dai kash, shima gogan nasa ran yake son kwata karfi da yaji dan ya shiga ba zai fito da dadin rai ba Wasa wasa ya dauki lokaci mai tsayi yana ibada, har sai da ta fara daukewar numfashi sannan ya saki abinda ya rike ya samu lafiya , lafiyar dake daskare a jikinsa A hankali yake shafa kanta bayan ya janyota jikinsa, hannayensa kuwa sun fi zuwa ainahin sittin saba'in sunna kara girgizawa dan da ace zai samu burinsa kuma muradinsa a kasan zuciyarsa a yanzun shine ya sake maidata ruwa "Khausar?" Ya furta a hankali yana sake shafa bayanta Idan uwanta ta kara tankewa sosai zuciyarta na dokawa, ita kadai ta san azabar da take ji a jikinta, baban burinta ta samu ta kula da jikinta ba tare da kowa na kusa da ita ba Ajiyar zuciya ya sauke kasa kasa sosai yake iya jin zafin da jikinta ya dauka ga kuma irin ajiyar zuciyar da take saukewa, shi dai ya san bai karata ba, dan a hankali ya bi gudun karanta , ama kuma da zata bashi dama ya dubata da ya ji dadi ko dan hankalinsa ya kwonta, a sanyaye ya sake furta" i'm so sorry wife, zaki yarda in dauko gan in duba ki?" Khausar ta lumshe ido na godiyar Allah dan ta samu hanyar da zai fita ya bata waje ta kula da kanta A hankali ta gyada kanta dan ta tabatar masa yana iya daukowar sannan ta samu ta juya tana jan abin rufar da kyar tana jin jikinta nema yake ya dume da zafi haka kuma matsananciyar kunya na neman hannata sukuni Murmushi ya yi bayan ya daura tawul dinta sabo sannan ya fita hankali kwonce ya nufi dakinsa yana jin wani irin sukuni da kwonciyar hankali a zuciyarsa da jikinsa baki daya Da kyar ta iya mikewa da dafewar bango ta karasa ta rufe dakin nata da ky sannan ta nufi bayi direct ta kunna ruwa masu zafi ta samu ta shige ta zauna bayan ta yi tsarki ta lumshe idannuwanta A hankali ta dafe wajen kirjinta tana jin wasu irin hawaye Masu dumi da daraja na zubowa daga gefen idannuwanta 'ya Allah, ya arahaman' ta ayana a cen kasan zuciyarta A hankali ta sake lumshe idannuwanta tana jin wani irin emotion mai girman gaske 'ashe dama kana so na?, Ashe kai ne mijina nake lalube? Ashe har kana iya maidani iyalinka cikin ruwan sanyi? Me yasa kana kallona ka kyaleni kana rakani a kulun ina kuka *DA CIWO A ZUCIYATA?*, shin tarin rashin hankalina ya hannaka sanar min ko kuwa gani kake yi Ni din ba cikakkiyar budurwar da za'a nemi soyayarta bane TAUFEEK?,' a hankali ta sake lumshe idannuwanta, dan abu biyu ne suka taru suka hade mata lokaci daya A gaskiya tana cikin farin ciki mai girman gaske na samun kanta a cikin wannan hali dan ta san wanda ya amshi budurcinta koda ba so zai zama bango a gareta dan ta san waye shi gashi kuma kafin hakan ya wakana ya furta mata kalma mai girman gaske da ya sake kwontar mata da hankali, watau dai gannin wannan rana da ta jima da sakawa ranta cewa ba zata ganta ba a gidan duniya sai kuma dayar maganar da ta tsaye mata a rai wace take tuhumar kanta da tunanin ta yiwu itace da kanta ta janyowa kanta wannan damuwa sakamakon wasu abubuwan da take yi wa'inda ta yiwu sunne suka saka TAUFEEK kasa tunkararta yake kallonta har sai da haka ta kasance da su? Lalle kuwa zata yi iya yinta dan gannin ta yaki ainahin nutsuwarsa da dukkan wani tunaninsa A yanzu ne zata yi anfani da baiwar da Allah ya yi mata dan gannin ta ainahin amshi tunaninsa, motsinsa, da dukkan wani abin da ya rage masa Ya furta mata kalmar so a gadonsu, in sha Allah sai ta ji shi daga bakinsa a wajen da babu gadonsu Ajiyar zuciya ta yi ta saukewa, ta yi namijin kokarin da ta kula da kanta sosai da sosai da kuma Allah ya taimaketa ta zamto likita ba sai an koya mata yadda zata kula da kanta ba Ta jima a bayin nan sai da ta ji ta gamsu ta mike dan tsaftace jikinta ta hanyar yin wankan janaba A daidai lokacin da take cikin bayi, a lokacin ne TAUFEEK ya dawo kofarta ya dakata ya murda da nufin budewa dan ya je ya taimaketa, domin shi da kansa ya san ya mata zuwan da bai yiwa Yumnah ba, ya kuma zauna ya more iya morewa, sai dai yana murdawar ya ji kofar a garkame Dan dakatawa ya yi bayan ya buga kadan yana jira ta bude masa, a lokacin kuwa ita tuni tana bayi, sai dai shiru dai bata bude ba Sake bugawa ya yi wannan karron bugawar da dan karfi ama kuma ba sosai din nan ba ya sake dakatawa yana sauraro dan baya tunanin zai iya juyawa ya barta a halin da ya mike ya barta Karar bude kofar Yumnah ya saka shi juyawa bangaren da Yumnar ta bude ta fito tamkar an jefota Dakatawa ta yi tana kallonsa tamkar wace ke son karantar wani abu a jikinsa tun daga kan tawul din dake kugunsa har zuwa abinda ke hannunsa wato akwatinsa ta asibiti "Yayanmu me kake yi a nan?" Yumnah ta fada cikin rasa tambayar da ya dace ta masa kirjinta na dokawa tana sake nufo inda yake tsayen Da mamaki yake kallonta jin tambayarta, sai kuma ya daure fuska dan ya san wacece ita yanzu zata yi kokarin zuba masa wata diramar cikin launukan diramominta Fuskar tasa a haden nan ya ce" [7/29, 9:22 PM] +234 806 191 8478: 💔💔💔💔❤‍🩹❤‍🩹💔💔💔💔 *DA CIWO A ZUCIYATA* 💔💔💔💔❤‍🩹❤‍🩹💔💔💔💔 _MALLAKIN_ *SAJIDA NIJAR* *FREE BOOK NE* 5️⃣6️⃣ *GARABASA, GARABASA, PROMOTION, PROMOTION DIN LITATAFAN MARUBUCIYAR A KAN FARASHI MAI SAUKI 1K, YAN NIJAR KUWA 1000 FRANCS CEFA* 1: Duk karyar kada 2: Yar mahaukaciya 3: Neman na kaina 4: Bani da zabi 5: Bak'a ce 6: Kutkale 7: Makauniya ce 8: Mage 9: Duk nisan jifa 10: Idan ka raina inda kake 11: Dutse 12: Alkalamin kadarata 13: Bani da zabi 14: Dakika Biyar 15:Wata kokowar 16: Aure yakin mata 17: Ni zan ladabi 18: Daga tafia daukar soja *Dukansu a kan farashi mai sauki, zaka saka dubu guda ne domin promotion ne nake yi, ka tuntubeni kan layina kamar haka +227 93 81 16 18, Sajida Nijar* Now *Da CIWO A ZUCIYATA* *Tallah, tallah, tallah* *SECRET DE LA FEMME DU MANGA* _Gidan Kamshi, Sirrin Manyan Mata, nesa tazo kusa,Amarya ,Uwar gida,Ango da mai gida Har ma da yan mata da samari shin kuna sane da cewa HAJIYA FUSAM ta shirya tsaf domin gwangwaje ku da turarakunta masu dankaran kamshi? Tare Kayan gyaram jiki na musamman ,wanda daga nesa kamshin ki kadai ya wadatar ya isar da sakon zuwanki waje,gidan ki kuwa sai ya zam abun kwatance wajen kamshi, kar na cika ku da surutu bara in fara zayyano su_ Farar Humura Bakar Humura Humura special, humura de bain Humura epicé Lait de nuit Parfums désodorisant Parfums rideau et dras Lait de nuit Alkam Kulakcam *Waɗannan kadan ne daga bangaren turaran ruwa* Gagab, sandal flex, Durot, durus, sandal fleur, tafarce, farce, sandal bangui, sandal, hypotonic sandal, al'ut, coktail creation VIP, Gajiji, Mankaji, turaran wutar labule da cafet, Aba malan, boulettes *Munada bangaren gyaran jiki kamar haka:* mai mai saka santsin jiki, mai mai kanshi, Kayan gyaran jiki mai saka fata ta yi santsi da laushi, kayan gyaran jiki mai saka fata ta yi fari, Sabulu mai saka fata ta yi haske, sabulu mai saka fata ta yi santsi, sabulu mai goge yanayin fata, mai wanda baya saka fari mai gyara fata Sayen na gari mai da kudi gida,sai an gwada akan san na kwarai💃💃 Hajiya Fusam na zaune a kasar Niger domin yin magana da ita kai tsaye tuntuɓi wannan number 97 82 44 94 *SECRET DE LA FEMME DU MANGA* Gidan Kamshi, Sirrin Manyan Mata💃💃💃💃💃 Tallah 3 Hajiata, ke kin san rayuwar aure sai da anini, in babu jagab a babar eriya oga ya kama tofa yawu da neman yadda zai yi bawan Allah, idan kuma babar haja a bude ham ai ba labari oga sai dai ya shiga ya fito kamar ya shiga kofar ruwa😔, zo ki ji, a farashi mai rahusa zaki gwangwaje ki rike bakin Elhaji gudun tada yara, ama idan lamari ya yi lamari tsaf zaku karya gado☹️🫣 🔥💥🔥💥🔥💥🔥💥🔥💥🔥💥🔥💥 *HOHOHO WANI KAYA SAI AMALE, DON JAKI BAZAI 'DAUKA BA, INA MATA MASU BUK'ATAR 'DAGA DARAJARSU A WAJAN MAZAJENSU INA MATAN DAKE SHAN WULAK'ANCIN MIJI KO NA KISHIYA ,INA MATAN DAKESON ZAMOWA MOWA AGIDAJEN AURENSU TO ALBISHINRU MAMAN ZARAH YAR MUTAN SOKOTO TA SHIRYA TSAF DOMIN GABATAR MAKU DA ZAFAFAN KAYAN MATA MASU KYAU DA INGANCI WANDA BASUDA ALGUS ACIKI , AKWAI MAGANI DANAYI BINCIKE AKANSU DAN FARIN CIKIN MA'AURATA NAMU BA IRIN NASU BANE KAYAN MU NA DABAN NE NA ASALIN SAKKWATAWAN SHEHU MASU ABUN MAMAKI* 07034251528 kayanmu masu inganci ne masu ladaftar da kowane irin namiji Kad'an daga cikin abubuwan da muke dasu Ingantaccen maganin nono , Wanda zai gyara maki nononki donmin dawo da martaban nononki acikin kankanin lokaci komai lalacewarshi kuwa sauran bayani sai mun had'u pc +234 703 425 1528 Maganin hips (hips up) Wanda zai ciko maki da hips dinki su cika suyi bul bul ga laushi dasu k'ara suyi dass abun sha'awar kowane namiji Maganin infection Sha yanzu magani yanzu Yana fatattakar sanyi cikin kankanin lokaci magani ne na maza da Mata insha Allah kowane irin sanyi gareki kikayi amfani dasu anwuce wajan Ingantacce Kuma sahihin maganin k'iba Wanda Zaki ciko acik kankanin lokaci zakiyi kibar ki Yar dai dai misali ki huta Zama da Rama Baki rasa ci ba Baki rasa sha ba amma kullum Ana kallon cewa kinada matsala agidan aurenki saboda wannan ramar , Rama batayi ba Sam Yar uwa Sabulun wanka Kalolin sabulun tsarki Turaren tsugunno Turaren al'ajab Hatsabibin turare Da sauransu 07034251528 Kalolin gumba Gumbar Dabino Gumbar gero Gumbar madara Gumbar matsi Gumbar ukku bala'i Gumbar tada zaune tsaye Gumbar sabon budurci Gumbar sa buzu kuwa Gumbar aya da kwakwa Gumbar ridi Gumbar mazari Sarauniyar gumba 3in1 Da sauran kalolin da bansamu fadi ba, Kalolin gari Garin mallaka Garin hutar da malaminki dakan jaraba Dakan Amare Dakan Ni'ima Dakan kishiya in bakiyi bani waje Garin sa buzu kuwa Garin buje.sharkaf Garin Dan la'asar Yayan hadiya mai suna dan la'asar Original Dan goshi Original Dan goshi (sabon salo) Original man damo Original man ayu Kitsen damo Sirrin tafin kafa Sirrin farinjini na uwargida da amarya harma da yan mata Kwallin idonka idona Muna hada set na sirrin mallaka hajiya ba boka ba Mallam sai tarin sirrika kema kizama kowa agidan surenki Akwai hadin sabon budurci ga yarinyar data rasa budurcinta ta hanyar fyade ko yaudarar d'a namiji da izinin Allah akayi maki wannan hadin to an wuce wajan sauaran bayani sai mun had'u pc Kalolin tsumi Tsumin mallaka Tsumin jaraba Tsumin madarar ni'ima Tsumin tabaje Tsumin Amare Tsumin sabon budurci Tsumin nono rakumi Matan gaske Ruwan jaraba, Da sauran kalolin da ban fada ba Kalolin matsi da basuda illa ajikin mace sai dai ma sukara maki lafiyar Matsin Dan mannau Matsin mallaka Dan la'asar Sabon budurci Mak'alemata Mashahurin matsi Ukku bala'i Matsin uban budurwa Akwai gumba ta matsi wadda Shanta akeyi ga matan da basa son yin matsi Muna hada set ga wadda Allah ya jaranfa da matsalar fyade har yarasa budurcinta , muna hada mata kaya ingantattun don dawo da martabar ta, Hohohohoho in ana dara fidda uwa ake *Kyallen al'ajabi* babban sirrin mallaka mai abun al'ajabi mallaki naki don samun damar shiga cikin jerin mata masu fada aji a gidan mazajensu , KARKU manta da sunan maman zarah sokoto sayen nagari maida kudi gida 07034251528 ina maraba daku sayen daya ko sari ina Sokoto sannan ina aikawa kowane gari cikin aminci da yardar Allah Ga Wanda suke bukatar ganin kalolin kayana to suyi sarving number na suyimun magana nayi sarving number ku zaku dinga ganin kalolin kayana a status ngd sosai 07034251528 Maman zarah mabera SOKOTO Fuskar tasa a haden nan ya ce" Ban fahimci me nake yi a nan ba?" Yumnah ta sake binsa da kallo, hannunta har neman fara yin rawa yake yi, muryarta na hadewa ta ce" a'a, ganinka na yi kamar zaka shiga wanka, kuma sai na ganka a kofar dakin nan, ga kuma abin duba marar lafiya, ko waye ba lafiya?" Kansa ya sake maidowa inda take tsaye, yana kallonta ya ce" Ba wanka zan shiga ba, nan din kuwa ko kin manta dakin Khausar ne? Ko bani da ikon zuwa inda matata take? Look Yumnah ki koma dakin ki bana son neman magana!" Yumnah ta jinginu da jikin garu, a hankali ta dora hannayenta saman kanta tana kallonsa, niyarta ta fashe masa da ihu ne ko kuka? Allah masani, Akwatin dake hannunsa ya ajiye ya karaso inda take tsaye ya sureta da ɗaukan da ya saka ta zarro idannuwa tana kallonsa Bai direta ko'ina ba sai saman kujera , rai bace yana dubanta ya ce" Kin rantse sai kin dagawa kanki hankali? Fine zaki samu abinda kike so, ki zauna a nan ki sake bude kunnenki da kyau zaki fi jiyowa jiyowa, tunda baki san cewa rarashinki da nake yi na tsoronki ya saka ba sai ki gyara zama, shirmen banza da wofi!" Rai bace ya fice ya bugo mata kofar da karfi ya sake komawa kofar dakin Khausar ya tsaya ya shiga bugawa wannan karron da karfi sannan ya bude bakinsa ya ce" Rufe dakin kika yi?" Khausar dake bakin madubi tana tsane kitsonta ta juyo da sauri tana hangen kofar tana kuma jin amon muryarsa kamar ya yi sama sosai "Khausar da ke nake fa?" Ya sake fada ransa na neman bacewa Khausar ta tabe baki ta ki zuwa ta bude din, juyawama ta yi ta ci gaba da kimtsa kanta ta karasa ta dauki ledar abincin da ta gani ajiye ta je ta zauna a hankali tana karkacewa ta bude ta shiga ci a hankali tana ta tsaraw kanta irin zaman da zata yi da su baki dayansu daga yau din nan "Ama ai kin ga lokacin ko? Ina kike so na je na kwana ne?" Ya fada wannan karron a sanyaye yana duban kofar yana ji tamkar ya bace ya ganshi a cikin dakin dan zai so ya rungumeta kamar yadda ya mata alkawari abinnan a bakinsa har garin Allah 6a waye, gashi tuni karfe hudu ce ke neman yi dan bakin ciki sunna neman bata masa rai Ya jima tsayen nan, da haushi haushi ya ce" Karma ki bude, Khausar nace karma ki bude dakin, aikin banza na tafi!" Ya yi shiru yana sauraro ko zata bude, karshema sai ya ga Khausar ta kashe fitilar dakinta, wato shi ta bari a titi daure da zani? Lalle ! Da haushi haushi ya yi dakinsa ya je ya zauna ya shiga buga wayar Alhusain Alhusain dake zaune a daidai lokacin su dare ne ama ba dare sosai ba yana shan shayinsa ya zubawa kiran ido dan ya san yanzu dai karfe hudu ce a kasan su TAUFEEK, dan haka da gagawa ya daga kiran yana fadin " Asalamu alaikum, freind lafiya? Waye ba lafiya?" "Nine Khausar zata bari a kofar daki daure da tawul? Kuma nine Yumnah zata nemi rainawa wayo? In takamarta ciki tunaninta zata ringa neman shiga hakina bayan Ni ina yin iya yina dan gannin na fita hakinta na kiyaye dukkan damuwarta to karya ne, babu wanda ya isa ya hanna min rawar gaban hantsi a gidana !" Alhusain ya zarro ido ya mike yana barin inda matarsa ke zaune ya fita filin gidansa ya dafe tsatso ya ce" anma isa, da gidanka a Barka ka kwana a waje?" Taufeek ya ce" Gashinan ta koro Ni ta rufen daki!" "To kai ban ce maka ka ringa ajiyar ky biyu ba ko komai sai na yi ta nanatawa zaka fahimta?" Alhusain ya fada cike da takaici TAUFEEK ya masa shiru yana ta huci Alhusain ya ce" To ka saurareni in fa ka ringa yi da sauki rikitaka zasu yi, ita dayar in ka yarda ta san ka haukace a kanta ka fa shiga uku,ita kuma karamar nan gaskiya ya dace ka sakata a tsarin da ya dace, domin babu kyau abinda take yi, ko dan lafiyarta da kwonciyar hankalinta ta kauda idonta a kanka da abokiyar ZAMANTA, ko daya kar ka daya damar yi maka irin haka, gidanka ne su matanka ne, kana da damar leka daya idan ka yi niya dan k ga lafiyarta , kana da ikon kwonci a dakin matarka in ranar girkinta ne, ka kula da freind kar su fi karfin ka su haɗaka da ciwon kai!" Ya idasa fada yana watsa hannu dan gaskiya ba zai so a masu raini ba, ehe ba fa zasu dauki haka ba, kuma yana bayan boyewar da TAUFEEK ke yi na soyayar Khausar dan ba ita daya yake aure ba in har ta gane tana iya yiwa Yumnah wani neman fitina, dan mata komai tsufansu ba zaka raba su da halin yarinta ba, ita kuma Yumnah gaskiya abinda take yi bashi da wani anfani, dan shi tunda ya fada masa ta fadin nan ranar tarewar Khausar ya nuna masa ya fa yiwa tufkar hanci dan tsaf zata hanna shi zaman aure da Khausar dan ta ga tana dauke da ciki Sosai ya sake saka TAUFEEK hawa ya yi zamansa a dakinsa yana jin sun cuce shi, rana irin wannan ce zasu masa irin wannan zasu kula masa wannan kulun? Lalle mata ana ce masa yana da aiki bai yarda ba sai yanzu,, ita Khausar ko tausayin kanta bata ji ko? Ya gode Da wannan ya dan rintsa, gari na wayewa ya fito ya shirya tsaf ya fice bangaren Hajia A bangaren Yumnah kuwa a halin da take ciki mahaifiyarta ce ta tabatar mata zata zo ta dauketa su tafi gida, ba zata iya ba, da kuka ta kwana yanzu haka a kwonce take kanta tamkar zai rabe biyu, idan ta tuna hasashen ta kuwa sai ta ji kamar numfashinta zai dauke Khausar kam ta samu barci, domin ta sha panadol ta kuma yi kokarin ajiye tunaninta waje daya, garin Allah na wayewa kuwa bayan ta sauka daga saman salayarta ta sake komawa ta gasa jikinta sosai har sai da ta ji tana iya hada tafiyarta , ama ba zata iya yin doguwar tafiya ba Kimtsa kanta ta yi cikin riga da sket sannan ta dora hijab bayan ta daura dan kwali ta fito sai zuba kanshi take yi da kyar take tafiyar fa, ama bata jin zata iya zama hajia na cen ba lafiya, kuma tana so ta yi kiran gida yau kwananta nawa bata ji mama ba, su kuwa ko su nemeta irin sun yayetan nan ta tafi ko? A nutse ta karasa bangaren Hajiar Da salama a bakinta ta shiga bangaren na Hajia kanta a kasa tana kokarin kiyayewa idannuwansa, sai dai tana duban wajen hajia a lokacin da take kokarin dukawa idannuwansu suka sarke da junna Gabanta ne ya yanke ya fadi, da sauri ta rike kujerar da Hajia ke zaune kan TAUFEEK a saman cinyarta sunna fira ko nace tana masa fira shi kuwa sai hade rai yake ko um baya bata amsa Hajia da kula ta ce" Kula yar nan kar ki ruftu a kasa in gaza daga ki, tashi dauko tuwon cen ko zo ki ci , a frij din cen kuwa akoy maganin zahin nan dauko ki dankari isashe kin ji? Allah dai ya miki albarka cire hijabin mana kin ji yar albarka?" Yau ba wani gardama ko nuna jin nauyin nan mai girma Khausar ta cire hijabinta ta ajiye nan ta nufi frij din da Hajia ke magana Hankali kwonce ta dauko galan din ta dawo ta ajiye sannan ta dauko abincin ta zo ta ajiye ta kuma nufi kicin dan dauko plate Da sauri Hajia ta yi wuf ta duko dubanta dan ta ga inda TAUFEEK yake kallo, da sauri ya rintse idonsa a ransa ya ayana' kai na shiga uku Ni TAUFEEK ' Hajia ta dago kanta tana tabe baki ta kama kansa dake saman cinyarta ta karkata hanyar da TAUFEEK ya yi ta ce" Kai dila Ni ban san gidan ubanda kake kallo ba bayan nan ta bi" TAUFEEK ya rintse ido yana ji kamar ya fashe da kuka, shi ina zai saka ransa ne?, Sam Hajia bata son zaman lafiya A hankali ya idasa bin Khausar da kallo bayan ta zauna ta zuba abincin hankali kwonce bata ce da shi ci kanka ba ta shiga ci Baki ya tabe yana neman abinda zai sa ta mai magana, ita kuwa ta hare ta kuma ki kallonsa dan ba zata iya kallon nan nasa ba gaskiya, kunya na iya hannata rawar gaban hantsi bayan ta yi niyar da yardar Allah sai dai ta ci galaba a kan game din! Tsumin dake cikin galan ta zuba ba tare da ita ta san ko menene ba, TAUFEEK kuwa yana gani ya gane menene dan a gabansa ma Hajia ta dafa A hankali ya tsinci bakinsa da fadin " Baki cika kofin ba" Hajia ta yi tsuru tana kallonsa Baki ta tabe tana cire kai tana gunguni , so take yi ta yi magana ama ta ki yi dan yau tunda ya zo ta ji jikinsa zafi, bata so ransa ya bace a dole ta hadiyi maganarta Cen ta ce" Ni wai yaushe Khausara zata koma bakin aikinta?" Khausar ta dago da sauri tana sakin murmushi tana kallon Hajia, ta ki kallon TAUFEEK wanda ya dago kansa yana kallonta shima TAUFEEK ya gyada kai ya ce" Ba inda zata je, ke kin ga Hajia ki fa kiyayeni na fada maki!" Hajia ta saka hannayenta ta dage kansa ta ture ta ce" To uban mai kwanoni wato marigayi mijina ko kuwa to uban dije, na kiyayeka ko ka kiyayeni, yarinya na aikinta ka wani zaunar da ita? To ba da Ni ba zata koma aikinta gobe goben nan" TAUFEEK ya zarro ido cike da mamaki ya ce" To ka ji mai kwanoni na ce to sannu matar mai kwanoni, ke babu inda matata zata je!" Hajia ta zabga masa harara ta ce" Matar auren dolen? Kai AMa baka da kunya, a nan fa kake min borin na maka auren dole?" Ido ya zarro yanzun kamar zai summe a zaune, da sauri ya kalli Khausar wace ta zuba masa itama sannan ya sake kallon Hajia Ji yake yi tamkar ya dagata ya yi juwa da ita ya saketa ta yi ta yawo a waje daya Kai innalilahi Rai bace ya mike yana gyara zaman yadin jikinsa ya ce" Babu inda matata zata je na fada in da wanda ta yiwa ciwo ya tanka in ji!" Khausar ta yi kamar bata wajen ta ci gaba da shan maganinta ama a zuciyarta kamar ta tambayeshi auren dole? Sai dai ta maze dan ta yiwa kanta alkawarin dole ta bambanta abokantaka da aure, dole ta nuna salo irin na matar gida ba kawar da za'a ringa rikici irin na ƙawance da junna ba! Du yadda ya so ta biye shi ya sauke abinda ke cikinsa ki ta yi, a dole ya yi tafiyarsa ya je ya shirya ya wuce office dan yana jin daf yake da fashewa Da yama tilis Khausar ta bar bangaren Hajia da abincinsu wanda ta girka a nan Hajiar ta saka ta dauko kwanoninta aka zuba nasu Jerewa ta yi saman table sannan ta shige dakinta Sallah ta fara yi bayan ta yi wanka sannan ta sake shiga cikin ruwan zafi Tana fitowa ta zauna ta shiga kimtsa kanta cikin nutsuwa Bakin wando dogo mai kama da roba ta saka bayan ta saka pant sannan ta saka riga fara kal mai dogon hannu , ita rigar sakakiya ce sosai dan har boturanta a bale suke su uku Turare ta shafa sosai tana tunanin a irgenta yau take fita a girki kamar yadda ake yi a al'adance Dan baby hijab ta saka fari kal wanda bakinsa wuyanta sai yan abin jikinsa da suka dan sauka daga bayanta kadan sannan ta rufe dakinta ta shiga sauka domin ta daidaici lokacin nan shine na shigowar TAUFEEK Tana saukowa ta nufi wajen zuba abinci, har ga Allah bata kula da Yumnah dake kwonce saman doguwar kujera ba, da ta gaisheta kamar yadda ta yi niyar du idan sun hadu zatana gaisheta ne da izinin ubangiji Yumnah kam da ido ta bi bayanta tamkar zata fado daga saman kujerar nan, A lokacin da take zuba abincinta cikin plate ya bude ya shi, sanye cikin sweet bakake sai farar riga tasss wace ta sake fitar da tsarin halitarsa da cikar izar da Allah ya bashi ya yi salama kasa kasa yana sauke hannunsa daga wajen kirjinsa da ya kai dan bale boturan rigar ta sama A hankali Yumnah ta juyo gabanta na faduwa, sai kuma ta juya da karfi ta kalli wajen Khausar wace itama salamar tasa ta sakata juyowa cike da nutsuwa ta nufo inda yake kasa kasa ta ce" 💔💔💔💔❤‍🩹❤‍🩹💔💔💔💔 *DA CIWO A ZUCIYATA* 💔💔💔💔❤‍🩹❤‍🩹💔💔💔💔 _MALLAKIN_ *SAJIDA NIJAR* *FREE BOOK NE* 5️⃣7️⃣ *GARABASA, GARABASA, PROMOTION, PROMOTION DIN LITATAFAN MARUBUCIYAR A KAN FARASHI MAI SAUKI 1K, YAN NIJAR KUWA 1000 FRANCS CEFA* 1: Duk karyar kada 2: Yar mahaukaciya 3: Neman na kaina 4: Bani da zabi 5: Bak'a ce 6: Kutkale 7: Makauniya ce 8: Mage 9: Duk nisan jifa 10: Idan ka raina inda kake 11: Dutse 12: Alkalamin kadarata 13: Bani da zabi 14: Dakika Biyar 15:Wata kokowar 16: Aure yakin mata 17: Ni zan ladabi 18: Daga tafia daukar soja *Dukansu a kan farashi mai sauki, zaka saka dubu guda ne domin promotion ne nake yi, ka tuntubeni kan layina kamar haka +227 93 81 16 18, Sajida Nijar* Now *Da CIWO A ZUCIYATA* *Tallah, tallah, tallah* *SECRET DE LA FEMME DU MANGA* _Gidan Kamshi, Sirrin Manyan Mata, nesa tazo kusa,Amarya ,Uwar gida,Ango da mai gida Har ma da yan mata da samari shin kuna sane da cewa HAJIYA FUSAM ta shirya tsaf domin gwangwaje ku da turarakunta masu dankaran kamshi? Tare Kayan gyaram jiki na musamman ,wanda daga nesa kamshin ki kadai ya wadatar ya isar da sakon zuwanki waje,gidan ki kuwa sai ya zam abun kwatance wajen kamshi, kar na cika ku da surutu bara in fara zayyano su_ Farar Humura Bakar Humura Humura special, humura de bain Humura epicé Lait de nuit Parfums désodorisant Parfums rideau et dras Lait de nuit Alkam Kulakcam *Waɗannan kadan ne daga bangaren turaran ruwa* Gagab, sandal flex, Durot, durus, sandal fleur, tafarce, farce, sandal bangui, sandal, hypotonic sandal, al'ut, coktail creation VIP, Gajiji, Mankaji, turaran wutar labule da cafet, Aba malan, boulettes *Munada bangaren gyaran jiki kamar haka:* mai mai saka santsin jiki, mai mai kanshi, Kayan gyaran jiki mai saka fata ta yi santsi da laushi, kayan gyaran jiki mai saka fata ta yi fari, Sabulu mai saka fata ta yi haske, sabulu mai saka fata ta yi santsi, sabulu mai goge yanayin fata, mai wanda baya saka fari mai gyara fata Sayen na gari mai da kudi gida,sai an gwada akan san na kwarai💃💃 Hajiya Fusam na zaune a kasar Niger domin yin magana da ita kai tsaye tuntuɓi wannan number 97 82 44 94 *SECRET DE LA FEMME DU MANGA* Gidan Kamshi, Sirrin Manyan Mata💃💃💃💃💃 Tallah 3 Hajiata, ke kin san rayuwar aure sai da anini, in babu jagab a babar eriya oga ya kama tofa yawu da neman yadda zai yi bawan Allah, idan kuma babar haja a bude ham ai ba labari oga sai dai ya shiga ya fito kamar ya shiga kofar ruwa😔, zo ki ji, a farashi mai rahusa zaki gwangwaje ki rike bakin Elhaji gudun tada yara, ama idan lamari ya yi lamari tsaf zaku karya gado☹️🫣 🔥💥🔥💥🔥💥🔥💥🔥💥🔥💥🔥💥 *HOHOHO WANI KAYA SAI AMALE, DON JAKI BAZAI 'DAUKA BA, INA MATA MASU BUK'ATAR 'DAGA DARAJARSU A WAJAN MAZAJENSU INA MATAN DAKE SHAN WULAK'ANCIN MIJI KO NA KISHIYA ,INA MATAN DAKESON ZAMOWA MOWA AGIDAJEN AURENSU TO ALBISHINRU MAMAN ZARAH YAR MUTAN SOKOTO TA SHIRYA TSAF DOMIN GABATAR MAKU DA ZAFAFAN KAYAN MATA MASU KYAU DA INGANCI WANDA BASUDA ALGUS ACIKI , AKWAI MAGANI DANAYI BINCIKE AKANSU DAN FARIN CIKIN MA'AURATA NAMU BA IRIN NASU BANE KAYAN MU NA DABAN NE NA ASALIN SAKKWATAWAN SHEHU MASU ABUN MAMAKI* 07034251528 kayanmu masu inganci ne masu ladaftar da kowane irin namiji Kad'an daga cikin abubuwan da muke dasu Ingantaccen maganin nono , Wanda zai gyara maki nononki donmin dawo da martaban nononki acikin kankanin lokaci komai lalacewarshi kuwa sauran bayani sai mun had'u pc +234 703 425 1528 Maganin hips (hips up) Wanda zai ciko maki da hips dinki su cika suyi bul bul ga laushi dasu k'ara suyi dass abun sha'awar kowane namiji Maganin infection Sha yanzu magani yanzu Yana fatattakar sanyi cikin kankanin lokaci magani ne na maza da Mata insha Allah kowane irin sanyi gareki kikayi amfani dasu anwuce wajan Ingantacce Kuma sahihin maganin k'iba Wanda Zaki ciko acik kankanin lokaci zakiyi kibar ki Yar dai dai misali ki huta Zama da Rama Baki rasa ci ba Baki rasa sha ba amma kullum Ana kallon cewa kinada matsala agidan aurenki saboda wannan ramar , Rama batayi ba Sam Yar uwa Sabulun wanka Kalolin sabulun tsarki Turaren tsugunno Turaren al'ajab Hatsabibin turare Da sauransu 07034251528 Kalolin gumba Gumbar Dabino Gumbar gero Gumbar madara Gumbar matsi Gumbar ukku bala'i Gumbar tada zaune tsaye Gumbar sabon budurci Gumbar sa buzu kuwa Gumbar aya da kwakwa Gumbar ridi Gumbar mazari Sarauniyar gumba 3in1 Da sauran kalolin da bansamu fadi ba, Kalolin gari Garin mallaka Garin hutar da malaminki dakan jaraba Dakan Amare Dakan Ni'ima Dakan kishiya in bakiyi bani waje Garin sa buzu kuwa Garin buje.sharkaf Garin Dan la'asar Yayan hadiya mai suna dan la'asar Original Dan goshi Original Dan goshi (sabon salo) Original man damo Original man ayu Kitsen damo Sirrin tafin kafa Sirrin farinjini na uwargida da amarya harma da yan mata Kwallin idonka idona Muna hada set na sirrin mallaka hajiya ba boka ba Mallam sai tarin sirrika kema kizama kowa agidan surenki Akwai hadin sabon budurci ga yarinyar data rasa budurcinta ta hanyar fyade ko yaudarar d'a namiji da izinin Allah akayi maki wannan hadin to an wuce wajan sauaran bayani sai mun had'u pc Kalolin tsumi Tsumin mallaka Tsumin jaraba Tsumin madarar ni'ima Tsumin tabaje Tsumin Amare Tsumin sabon budurci Tsumin nono rakumi Matan gaske Ruwan jaraba, Da sauran kalolin da ban fada ba Kalolin matsi da basuda illa ajikin mace sai dai ma sukara maki lafiyar Matsin Dan mannau Matsin mallaka Dan la'asar Sabon budurci Mak'alemata Mashahurin matsi Ukku bala'i Matsin uban budurwa Akwai gumba ta matsi wadda Shanta akeyi ga matan da basa son yin matsi Muna hada set ga wadda Allah ya jaranfa da matsalar fyade har yarasa budurcinta , muna hada mata kaya ingantattun don dawo da martabar ta, Hohohohoho in ana dara fidda uwa ake *Kyallen al'ajabi* babban sirrin mallaka mai abun al'ajabi mallaki naki don samun damar shiga cikin jerin mata masu fada aji a gidan mazajensu , KARKU manta da sunan maman zarah sokoto sayen nagari maida kudi gida 07034251528 ina maraba daku sayen daya ko sari ina Sokoto sannan ina aikawa kowane gari cikin aminci da yardar Allah Ga Wanda suke bukatar ganin kalolin kayana to suyi sarving number na suyimun magana nayi sarving number ku zaku dinga ganin kalolin kayana a status ngd sosai 07034251528 Maman zarah mabera SOKOTO Kasa kasa Khausar ta ce" Wa'alaika Salam, yauwa please rike min in Bala boturan rigana".....a hankali, cikin rada rada ta yi maganar, sai dai idannuwanta na sauka kan Yumnah ta ja ta tsaya daga niyar karasawa inda yake tsaye yana kallonta da wani irin kallo mai wuyar fasara Dan murmushi ta saki bayan ta dauke dubanta a kan Yumnah a juya ta nufi sam da plate din abincinta bata tsaya ta kara cewa komai ba, domin ba zata taba cin fuskar Yumnah ba, bata da wannan niyar, koda Yumnah na neman rainata ba zata bari su kona kawunansu a banza da wofi ba, idan har kishin ne zata fi so su yi mai tsafta ba irin wannan ba Sai kuma ta lumshe idannuwanta tana jin banbarakwai wai namiji da sunnan Hajara, yau itace ke batun kishin Besty? Murmushi ta saki ta gyara zamanta ta hanyar kwatanta daura kafa daya kan daya Ya fi a irga da take ɗorawa tana saukewa dan bata saba ba, sai dai ta tirsasa kanta ta dora din ta kuma zaunar da kafar a haka cikin nutsuwa ta shiga cin abincinta tana jin kewar iyayenta da kannenta har kasan zuciyarta A falon kasa kuwa da kyar Yumnah ta iya gaishe shi , domin tunda jinninta ya hau ta tsayar da dubanta a jikin Khausar ita da kanta ta ji ta sare hankalinta na neman idasa tashi Silalewa ta yi ta haye sama, cike da tsoron juya bayanta dan haka kawai ta saka a ranta cewar mai wancen zai kalli nata kuwa? A hankali TAUFEEK ya zauna yana ajiye wayarsa gefen kujera ya kai hannunsa daf da habarsa ya dan shafa yana murza sajen wajen tamkar wanda wajen ke masa kaikayi ko ciwo Idannuwansa ya daga ya sauke saman wayarsa ya dauki wayar ya amsa kiran da ke masa Dangane da aikinsa ne na makaranta da ya kwana biyu bai leka ba, nan ya gabatar da uzurinsa sannan ya ajiye wayar yana lumshe idannuwansa Yana ji a ransa cewar har yanzu bai idasa zama cikakken magidanci ba tunda har zai tashi ya sauko du su watse su barshi a nan Wata zuciya na rikirkirtashi idan ya yi tunanin rike mace biyun nan, anya kuwa wasan da zai iya ci gaba da bugawa ne? Ajiyar zuciya ya sauke ya mike direct ya karasa dakin Khausar wace ke zaune bayan ta gama ci ta rufe idannuwanta a kan kofar shigowar ta kasa fita dan bata an ko Yumnah na tare da shi ba ita kuma niyarta daban da ta da, dan ko ba komai ai shekarunta sun isa su bata damar damawa rashin samun wajen yin ne dole ta noke Da salama ya shigo yana sauke kaifafun idannuwansa a saman fuskarta A hankali ta sauke kafar nata dake daya saman daya ta yi iya yinta ta zuba nata dubanta itama a cikin nasa tana amsa salamar a saman lebenta sannan ta zuba masa ido har ya karaso ya zauna daf da ita kafin yake kai bayansa gaba daya ya kwonta saman bed din "Dan wajen kuwa ya kasance a bakina har garin Allah ya waye" amon muryarsa a jiya ya dawo dodon kunnenta a lokacin da take tunanin abinda ya dace ta fara gabatar masa Da sauri ta mike tsigar jikinta na tashi ta shiga sauke numfashi tamkar ta yi gudun tsira sannan ta juya da dan sauri ta nufi hanyar frij dinta ta bude ta dauko tataciyar madarar wajen hajia dan ita kam tana jin dadinta sosai ta dauki kofin dake zice ta riko ta karaso daidai lokacin da ya dan mirgino ya zuba mata ido yana kallonta Dakatawa ta yi dan daf da shi ta zuba hannunta na son kwasar rawa Murmushi ya saki hadi da ajiyar zuciya a hankali ya mika hannunsa ya riko kofin sannan ya mike tsayen da take ya zamto ya kere tsayinta ainun ya taho da hannun nata da kofin daf da bakinsa a hankali ya shiga sha yana lumshe ido Cikin rashin karfin jiki ta janye dubanta daga yadda yake lumshe idon cike da jin kunya ta dora duban nata a damtsen hannunsa dake mike daf da kugunta Hannunta ta so janyewa da nufin juyawa, a hankali ya saka hannun nasa ya janyota jikinsa ta hanyar janyo kugunta har sai da jikinsu ya hadu da dan karfi sannan ya dan sasauta mata ya tsareta da duban dake daf da kasarata Kasa kasa cen ta furta" Barka da saukowa , yaya gajiya?" A hankali ya dago habarta da ta yi furucin cen cikin makoshinta tamkar ba Khausar dinsa dake ihu in yana waje ba abinda ya dameta ba A hankali ya fitar da harshensa ya kawo daf da lebenta ya dan lasa yana kallon yannayinta Cike da jin kunya ta rufe idannuwanta da hannayenta biyu da suke dauke da jan lalle sannan ta nemi shigewa cikin jikinsa cikin dabara ta sake boye fuskarta a kirjinsa Ido ya zarro cike da mamaki yana kallonta lokaci daya zuciyarsa ta shiga dokawa Cen kasa kasa ta furta" maimakun ka huta zaka fara neman magana ko?" TAUFEEK ya lumshe ido yana jin kusoshin kansa na daf da kuncewa, gaba daya fushin da ya kunso da tunanin anya kuwa a bashi kula yadda ya dace suka gudu suka barshi da wani irin shauki mai wuyar fasara "Kunyana kike ji?" Ya samu harshensa da furta kalaman da ba ainahin su yake son fada daga bakinsa ba Bata bashi amsa da fatar baki ba, sai da kanta ta dan daga a hankali still tana jikinsa kanshin turarenta ya hade da nasa Ajiyar zuciya yake saukewa a jejere a hankali ya karasa wajen bed din nata da ita ya zauna ya dorata saman cinyarsa abaya ko jin nauyinta kasa kasa yake shafa hannayenta yana son dago fuskarta ya ce" Dama za'a ji kunyana?" Yanzunma bata ce masa komai ba, cikin dabara ya kai hannunsa saman cinyarta yana ji a ransa dole ya bita a hankali, sannu sannu ya ce" why kika rufe min kofa, bayan na san na yi barna? Ko nuna min za'a yi da likita fa na kwonta?" Har ga Allah yanzun kam ji ta yi kamar ta zura da gudu, dan har sai da ta so kwace kanta daga jikinsa ya kiya ya sake maidata ya rungumeta sosai a jikin nasa Cen kasan makogwaronta ta ce" Abinci fa?" Yanzun dagowa ya yi dan dole ya zubawa fuskarta ido, kai? Ya bani ya lalace, kamar ba ita ba A hankali ta samu ta mike daga jikin nasa tana jin yadda itama nata kirjin ke dokawa Da dabara ta samu ta rike kanta, cikin sabon salon yi masa magana ta ce" Abincin fa? Tashi mu tafi ka ci abinci urs bosss" 'Ya Salam ya ayana a kasan zuciyarsa A fili kuwa ji ya yi wani irin girma da isa na shigarsa 'dama na san tsarina ce, shi yasa ta zama zabina' ya sake ayanawa a zuciyarsa A bayane ya riko hannunta yana bin dima diman abinnan da kallo ya ce" Wai da in dan kashe arna kafin in ci abinci kin san lada ne da abin sosai anMatana" Murmushi ta yi ta janye hannunta ta karasa wajen tufafinta ta bude ta ciro hijab dogo ta zumbula sannan ta juyo inda yake zaune jiki a mace ta wani sakar masa fari da madaidaiciyar fuskarta da dara daram idannuwanta da suka dauki kwali a hankali ta ce" wa'inda ka kashema ai sun isa sir, taso mu je" Ido ya zarro yana binta da kallo har ta bacewa ganninsa Ajiyar zuciya ya sauke a ransa ya ayana' Ni da ban mutu ba, ai dole na raya sunna matata' Sai da ya je dakinsa a gagauce ya yi wanka ya cenza tufafinsa sannan ya je ya tiso keyar Yumnah suka sauko dan har yanzu basu yi wani zaman a zo a gani ba A wajen cin abincin Khuausar ta zubawa kowa bayan ta ji ra'ayinsa ita kuma ta zuba jus kadan tana dan sha tana tunanin abinda take son tambayarsa dan ta ci nata abincin har suka gama ya masu umarnin zama a falo Bayan ya zauna din shima ya fuskance su, da yannayin cikakken magidanci ya yi masu salama sannan ya ce" Ina son yin magana da ku, bana son kowa ya katse Ni da abin bacin rai ko na raini wa junnanmu, ina fatan kun fahimta?" Su dukansu sun bashi hankalinsu ne kuma sun amsa shi, dan bai bada fuskar raini ba ko kadan Da kula ya ce" ina so ku fahimceni ku kuma dauko maganana da mahimmanci kamar yadda na dauke ku da mahimmanci, ina so kowace ta sani gidan aure take, zaman aure muka taru mu yi wanda nake fatan ya zame mana sanadiyar shiga aljanna, dole ne ku koyi hakuri da junna, dole ne ku iya kaudawa junna kai a wasu abubuwan dan a zauna lafiya, hakan na nufin ya shafi kowa ba maganar karantar shekaru ko girman shekaru a gidan aure, dan du wace ta iya daukan namiji tana cikin layin wace Allah zai kama idan ta cutawa yar uwarta dan son rai" Dakatawa ya yi yana kai dubansa wajen tv ya kashe ya sake maido dubansa kansu, yanzunma da yannayin serius ya ci gaba da fadin" kowace nan ra'ayina ne, babu wace aka min dole ko aka cusa min, ina so ku san ina iya zaman aure da ku ne dan ina son ku!" Su dukansu sai da suka kalle shi wannan karron sannan suka kalli junna, shi kuwa ya yi kamar bai ga abinda suka yin ba ya ce" Dan haka ina so kokowarku ta zamto dan ku gyara zaman mu ba dan daga min hankali ba " Khausar ta turo baki sosai tana dane kanta, dan har ga Allah bata taba jin wani guguwar balaki irin na yanzu ba, kuma abin haushin a kan gaskiyarsa da yake magana ba karya ba, da kyar ta dauke kanta ta sada kasa tana jin lokacin da yake tambayar shin me suka tsaida maganar kwana? Yumnah kanta kasa furta a ta yi, zuciyarta tafarfasa kawai take yi tunda ya fara magana yana nuna darajar su daya a zuciyarsa abin ya nemi zautar da tunaninta "Magana nake yi" TAUFEEK ya fada a nutse yana sauke masu duba Da kyar Khausar ta iya jan numfashi gannin Yumnah ba magana zata yi ba ta ce" Du yadda aka yanke tunda ai yau nake fita a girki Ni du daya ne" TAUFEEK ya kalleta da mamaki ya ce" Kamar yaya fa fita a girki yau?" Khausar ta dube shi, sai kuma ta sada kanta a hankali ta ce" Eh, ai gobe in sha Allah ya kama sati daya cif da daura aurenmu" Taufeek ya sake zuba mata ido yana ayana'ka ji yar bakin ciki, yau Ni na ga bakin ciki a wajen yar gidan Aba ' A bayane kuwa a nutse a kuma tausashe ya ce" to ai goben ne yake kamawa kwana hudu da tarewarki, hakan na nufin sauranki kwana uku ko Besty AM?" Yumnah ta dago kai da sauri, yanzun kam sai da ta ji bakinta na fadin" A'a, ai tunda ya kama sati ta fita a aiki sai mu dawo yin kwana ɗaya daya da girki!" Taufeek ya zuba mata ido, ya sake maida dubansa kan Khausar Lalle ya gane cewa koda zai bi su a laluma dan zaman lafiya da kuma daukan daraja irin na iyalinsa, sai ya nuna masu kuma shine mijin su matansa ne Rai hade ya ce" Ku yi hakuri da jinna shiru rubutu gayanan dai, ina busy ne sorry😍😍😍😍😍 💃🏻💥💃🏻💥💃🏻💥💃🏻💥💃🏻💥 *ALBISHIRINKU MATAN AFRICA DA KEWAYE SHIN KUNADA LABARIN SHAHARARRA KUMA GOGAGGIYAR MAI SAIDA KAYAN MATAN NAN WATO MAMAN ZARAH SOKOTO IN BAKIDA LABARINTA TO MATSO KUSA KIJI* *_maman zarah Mai kayan Mata sokoto ta shahara wajan kawo maku ingantattun Kayan Mata masu matuk'ar kyau da inganci ta yadda cikin sauki ba boka ba malam Zaki ja ragamar maigidanki yadda kikeso kayane naji da Fadi da kudi kalilan ki zama tauraruwa 💥a zuciyar mijinki ,ba kalan kayan matan da bamuda shi kedai nemi maman zarah sokoto don gyara kanki ciki da waje karku manta mace Mai gyara kanta Bata boranci,maman zarah sokoto kayanmu daban ne , nememu ta wannan number don samun Karin bayani_* 07034251528 [8/2, 7:46 PM] +234 708 653 0343: 💔💔💔💔❤‍🩹❤‍🩹💔💔💔💔 *DA CIWO A ZUCIYATA* 💔💔💔💔❤‍🩹❤‍🩹💔💔💔💔 _MALLAKIN_ *SAJIDA NIJAR* *FREE BOOK NE* 5️⃣8️⃣ *GARABASA, GARABASA, PROMOTION, PROMOTION DIN LITATAFAN MARUBUCIYAR A KAN FARASHI MAI SAUKI 1K, YAN NIJAR KUWA 1000 FRANCS CEFA* 1: Duk karyar kada 2: Yar mahaukaciya 3: Neman na kaina 4: Bani da zabi 5: Bak'a ce 6: Kutkale 7: Makauniya ce 8: Mage 9: Duk nisan jifa 10: Idan ka raina inda kake 11: Dutse 12: Alkalamin kadarata 13: Bani da zabi 14: Dakika Biyar 15:Wata kokowar 16: Aure yakin mata 17: Ni zan ladabi 18: Daga tafia daukar soja *Dukansu a kan farashi mai sauki, zaka saka dubu guda ne domin promotion ne nake yi, ka tuntubeni kan layina kamar haka +227 93 81 16 18, Sajida Nijar* Now *Da CIWO A ZUCIYATA* *Tallah, tallah, tallah* *SECRET DE LA FEMME DU MANGA* _Gidan Kamshi, Sirrin Manyan Mata, nesa tazo kusa,Amarya ,Uwar gida,Ango da mai gida Har ma da yan mata da samari shin kuna sane da cewa HAJIYA FUSAM ta shirya tsaf domin gwangwaje ku da turarakunta masu dankaran kamshi? Tare Kayan gyaram jiki na musamman ,wanda daga nesa kamshin ki kadai ya wadatar ya isar da sakon zuwanki waje,gidan ki kuwa sai ya zam abun kwatance wajen kamshi, kar na cika ku da surutu bara in fara zayyano su_ Farar Humura Bakar Humura Humura special, humura de bain Humura epicé Lait de nuit Parfums désodorisant Parfums rideau et dras Lait de nuit Alkam Kulakcam *Waɗannan kadan ne daga bangaren turaran ruwa* Gagab, sandal flex, Durot, durus, sandal fleur, tafarce, farce, sandal bangui, sandal, hypotonic sandal, al'ut, coktail creation VIP, Gajiji, Mankaji, turaran wutar labule da cafet, Aba malan, boulettes *Munada bangaren gyaran jiki kamar haka:* mai mai saka santsin jiki, mai mai kanshi, Kayan gyaran jiki mai saka fata ta yi santsi da laushi, kayan gyaran jiki mai saka fata ta yi fari, Sabulu mai saka fata ta yi haske, sabulu mai saka fata ta yi santsi, sabulu mai goge yanayin fata, mai wanda baya saka fari mai gyara fata Sayen na gari mai da kudi gida,sai an gwada akan san na kwarai💃💃 Hajiya Fusam na zaune a kasar Niger domin yin magana da ita kai tsaye tuntuɓi wannan number 97 82 44 94 *SECRET DE LA FEMME DU MANGA* Gidan Kamshi, Sirrin Manyan Mata💃💃💃💃💃 Tallah 3 Hajiata, ke kin san rayuwar aure sai da anini, in babu jagab a babar eriya oga ya kama tofa yawu da neman yadda zai yi bawan Allah, idan kuma babar haja a bude ham ai ba labari oga sai dai ya shiga ya fito kamar ya shiga kofar ruwa😔, zo ki ji, a farashi mai rahusa zaki gwangwaje ki rike bakin Elhaji gudun tada yara, ama idan lamari ya yi lamari tsaf zaku karya gado☹️🫣 🔥💥🔥💥🔥💥🔥💥🔥💥🔥💥🔥💥 *HOHOHO WANI KAYA SAI AMALE, DON JAKI BAZAI 'DAUKA BA, INA MATA MASU BUK'ATAR 'DAGA DARAJARSU A WAJAN MAZAJENSU INA MATAN DAKE SHAN WULAK'ANCIN MIJI KO NA KISHIYA ,INA MATAN DAKESON ZAMOWA MOWA AGIDAJEN AURENSU TO ALBISHINRU MAMAN ZARAH YAR MUTAN SOKOTO TA SHIRYA TSAF DOMIN GABATAR MAKU DA ZAFAFAN KAYAN MATA MASU KYAU DA INGANCI WANDA BASUDA ALGUS ACIKI , AKWAI MAGANI DANAYI BINCIKE AKANSU DAN FARIN CIKIN MA'AURATA NAMU BA IRIN NASU BANE KAYAN MU NA DABAN NE NA ASALIN SAKKWATAWAN SHEHU MASU ABUN MAMAKI* 07034251528 kayanmu masu inganci ne masu ladaftar da kowane irin namiji Kad'an daga cikin abubuwan da muke dasu Ingantaccen maganin nono , Wanda zai gyara maki nononki donmin dawo da martaban nononki acikin kankanin lokaci komai lalacewarshi kuwa sauran bayani sai mun had'u pc +234 703 425 1528 Maganin hips (hips up) Wanda zai ciko maki da hips dinki su cika suyi bul bul ga laushi dasu k'ara suyi dass abun sha'awar kowane namiji Maganin infection Sha yanzu magani yanzu Yana fatattakar sanyi cikin kankanin lokaci magani ne na maza da Mata insha Allah kowane irin sanyi gareki kikayi amfani dasu anwuce wajan Ingantacce Kuma sahihin maganin k'iba Wanda Zaki ciko acik kankanin lokaci zakiyi kibar ki Yar dai dai misali ki huta Zama da Rama Baki rasa ci ba Baki rasa sha ba amma kullum Ana kallon cewa kinada matsala agidan aurenki saboda wannan ramar , Rama batayi ba Sam Yar uwa Sabulun wanka Kalolin sabulun tsarki Turaren tsugunno Turaren al'ajab Hatsabibin turare Da sauransu 07034251528 Kalolin gumba Gumbar Dabino Gumbar gero Gumbar madara Gumbar matsi Gumbar ukku bala'i Gumbar tada zaune tsaye Gumbar sabon budurci Gumbar sa buzu kuwa Gumbar aya da kwakwa Gumbar ridi Gumbar mazari Sarauniyar gumba 3in1 Da sauran kalolin da bansamu fadi ba, Kalolin gari Garin mallaka Garin hutar da malaminki dakan jaraba Dakan Amare Dakan Ni'ima Dakan kishiya in bakiyi bani waje Garin sa buzu kuwa Garin buje.sharkaf Garin Dan la'asar Yayan hadiya mai suna dan la'asar Original Dan goshi Original Dan goshi (sabon salo) Original man damo Original man ayu Kitsen damo Sirrin tafin kafa Sirrin farinjini na uwargida da amarya harma da yan mata Kwallin idonka idona Muna hada set na sirrin mallaka hajiya ba boka ba Mallam sai tarin sirrika kema kizama kowa agidan surenki Akwai hadin sabon budurci ga yarinyar data rasa budurcinta ta hanyar fyade ko yaudarar d'a namiji da izinin Allah akayi maki wannan hadin to an wuce wajan sauaran bayani sai mun had'u pc Kalolin tsumi Tsumin mallaka Tsumin jaraba Tsumin madarar ni'ima Tsumin tabaje Tsumin Amare Tsumin sabon budurci Tsumin nono rakumi Matan gaske Ruwan jaraba, Da sauran kalolin da ban fada ba Kalolin matsi da basuda illa ajikin mace sai dai ma sukara maki lafiyar Matsin Dan mannau Matsin mallaka Dan la'asar Sabon budurci Mak'alemata Mashahurin matsi Ukku bala'i Matsin uban budurwa Akwai gumba ta matsi wadda Shanta akeyi ga matan da basa son yin matsi Muna hada set ga wadda Allah ya jaranfa da matsalar fyade har yarasa budurcinta , muna hada mata kaya ingantattun don dawo da martabar ta, Hohohohoho in ana dara fidda uwa ake *Kyallen al'ajabi* babban sirrin mallaka mai abun al'ajabi mallaki naki don samun damar shiga cikin jerin mata masu fada aji a gidan mazajensu , KARKU manta da sunan maman zarah sokoto sayen nagari maida kudi gida 07034251528 ina maraba daku sayen daya ko sari ina Sokoto sannan ina aikawa kowane gari cikin aminci da yardar Allah Ga Wanda suke bukatar ganin kalolin kayana to suyi sarving number na suyimun magana nayi sarving number ku zaku dinga ganin kalolin kayana a status ngd sosai 07034251528 Maman zarah mabera SOKOTO Rai a hade ya ce" Yau kwananki uku a gidanki, saura kwana hudu cif ki fita a girki" Daga haka ya juya ya kunna tv din nan ya kai tashar labaru ya shiga kallonsa ya kyale su Kowace shiru ta yi, jifa jifa sai daya ta saci kallonsa ko na yar uwarta har dai suka dan dauko lokaci Yumnah ta mike ta dube shi ta ce" good night yayanmu" Dubanta ya yi shima , da kula ya sakar mata murmushi sannan ya lumshe mata ido a tausashe ya ce" Har kin gaji da firar?" Da kyar ta iya gyada kai tana jiran gannin ya miko mata hannu ya rungumata kamar yadda ya mata a kwanakin da Khausar din ta shigo, bata san ya riga ya dauki dukan tsaron da zai ringa yawan saka shi surutu tsakaninsa da su ba, in sha Allah ko a kan Khausar zai yi iya yinsa ya fita hakin Yumnah A tausashensa ya ce" Good night wifey" Yumnah ta hadiye yawun dake wuyanta ta juya ta haura sama ta nufi dakinta Tana shiga jikinta har rawa yake yi ta dauki wayarta ta shiga kiran numbar mahaifiyarta Yayarta ce ta dauka dan maman nasu ta shige daka dan kwontawa domin bata jin dadin jikinta A tausashe ta yiwa Yumnah salama wace tana hannun an daga ta fashe da kuka Yumnah ta yi dif da kukanta tana jin Muryar yayarta dan ta sani ne banda fada babu abinda zata yi mata, domin shekaran jiya cewa ta yi zata zo ta zaneta ko ta fadawa abansu bata kwontar da hankalinta ba Cike da tausayawa Akilah ta ce" Yumnah kuka ne kike yi? Me yake damunki kanwata?" Yumnah na jin yannayinta , ama ta kasa fitowa fili ta fada mata abinda yake damun nata dan gani take yi ba zata gane komai ba tunda har take kallon auren TAUFEEK a daidai ne "Yumnah?, Ki fada min damuwarki kin ji kanwata? Shin kina da wanda zaki fadawa ne sama da Ni? Baki da lafiya ne? Menene um? Sanar min" Akilah ta karasa fada da kula da kuma tausasawa Yumnah ta ja numfashi, a hankali ta saki kukanta kasa kasa sosai tana murzar hannunta ta ce" Aunty, na kasa sakawa zuciyata salama da maganar auren nan, Ni na san ba zai taba bani kulawar da yake iya bata ba, idan kuma ya zama abu daya da ita Ni na san na zama banza a gabansa dan ta ko ina ta fi Ni power a duniyarsa" Cike da tausayawa Akilah ta ce" Ya Allah, haba Yumnah me yasa kika ce haka? " Yumnah ta ja numfashi ta ce" Aunty Ni na san haka ne, ban taba gannin wanda zasu yi masifa da shi murya sama sama ba ya dawo yana kokarin ganin farin haƙoransa ba sai ita, domin ko a da da muke soyaya idan ya yi fushi ma gaza shawo kansa ina fada mata a waya zata ce sai ya zo inda nake ki ganshi ya zo din, a da da take nesa da shi bale yanzu?" "Yumnah ki dan dakata da wannan dogon bayanin dan kima neman sakani a damuwa, ina son Sannin wulakantaki yake yi ne yanzun ko mene?" Akilah ta katse ta dan bata son dogon shiga details din nan, haka kawai take ji a ranta bata so Yumnah ta ce" Aunty, Ni bai min komai ba, ama ina mai tabbatar maki zai min din ne, dakinta fa na ganshi zai shiga daure da tawul" Akilah da mamaki ta ce" Ke bai taba shiga naki dakin ba kennan?" Yumnah ta ce" Yana shiga, yana shigowa, a yannayin da na ganshi ne ya tsoratani kamar wanda ya yi having s ......" "Yi shiru dan Allah" Akilah ta fada a sanyaye tana katse mata hanzarin son fayace wasu abubuwan da bai dace ta fito ta fada kai tsaye ba A tausashe Akilah ta ce" Bayan wannan laifin wane da wane kuma ya maki yar kanwata?" Yumnah ta sake gyara zamanta ta ce" Aunty, dazu wai ya mana rabon kwana, shi da kansa fa, yace wai bata gama satin amarci ba bayan ita da kanta ne tace ai ta cika sati da daurin aurensu yau, sai kawai cewa ya yi bata cika ba ya hade fuska ya mana banza, Aunty sonta yake yi ko? So yake ya wulakantaki ko aunty?" A sanyaye sosai Akilah ta ce" Aa, ba maganar wulakanci a nan, Yumnah dan Allah zamu iya yin magana da ke ta fahimta? Kin min alkawarin saurarata da kuma kokarin yiwa kanki adalci ta hanyar kwatanta shawarwarina?" Yumnah ta yi tsai tana shan jinnin jikinta, sai dai yadda auntyn nata ke yi mata magana a tausashe ta saka a ranta cewar zata iya yi mata magana mai dadi yau A nutse sosai Akilah ta ce" Kanwata, ina so ki san cewa a duniya kowa yana rayuwa ne da son ransa, sai dai idan ka yi kokari ka yi anfani da hakan ta hanya mai kyau zaka ji dadi, Yumnah, ya dace ki kwatanta abinda kike ji a kan Khausar, itama mutun ce, mai rai da lafiya, wace ya dace a tausayawa fiye da kowa ko dan shekarun da ta dauka bata samu miji ba, ki sani itama tana da zuciya a kirjinta kuma zata so a so ta a kuma kyautata mata, Yumnah baki san irin tsakaninta da mijinku ba, ama har yanzu ban ji inda kika ce ta maki ba daidai ba, ko marin da mama ke fadawa dad cewar ta maki da aka bi sila a kanki fadan ya sauka dan kece kika yi abinda kika jama kanki haka, Yumnah ita rayuwa tun ana rakiyarka kar ka ja a dawo daga rakiyarka, ki sani mijinki mai adalci ne domin a irin yadda kike zuba masa abubuwa da wani ne da tuni an yi dayan biyu, ko karamar bazawara ko ya maisheki ba kowa ba a gabanki ya aikata abinda ya san zai iya dauke numfashinki, ki sani ba tsoronki zai sa a so ki ba, a'a sai dai biyayarki, idan takamarki kuwa kina dauke da cikinsa ki taka a sannu itama wace ya auro tana iya dauka, Haba Yumnah sai kace ba yar musulmai ba? Ina karatunki? Mama tace yace ya raba maku gida kin kiya, to me kike so ne a maki a rayuwa? Haba Yumnah kin san da ba so da ba zai daga maki kafa ba, mijinki baban mutun ne, ban kara jin ina shakarsa ba sai a asibiti, shikenan ke sai ki ringa wulakanta masa zuciya? Yaya zaki budi baki ki ce wai ya je dakin matarsa kuma ke da na tambayeki bai taba shiga naki dakin ba hankali kwonce kin shaida min yana shiga , shin ita ba mutun bace? Haba Yumnah ta yayama zaka sakawa namiji ido a kan shigarsa da fitarsa da matarsa? Idan ke aka sakawa yaya zaki ji ne?, Ya dace in kana abu ka ringa saka lisafi ka kuma ringa tuna mutuwa, dukka kaf abubuwan nan da kike yi zaki tsaya gaban Allah ne ki yi bayani Yumnah, dole zaki tsaya ki yi bayani, ki tuna fa Allah yana yafe laifin da ka yi masa ne idan ka nemi yafiya ama baya yafe laifin da ka yiwa bawansa sai idan shi bawan nasa ne ya yafe maka, Yumnah shin bakya gannin wannan laifin a baba ko? Ki sani baban laifi ne dake iya kaiki halaka, kina ji kina gannin son zuciyarki zai kaiki halaka idan baki tuba ba" Akilah ta saurara har tana dubawa dan kar aje ita kadai ke zuba Yumnah ta kashe kiran , dan a yadda kanwar Tata ke nunawa ita abin har tsoro yake bata A tausashe ta ce" Yumnah kina fahimtana kuwa?" Yumnah dake share hawaye a hankali ta gyada kanta tana amsawa da eh "Mijinki yana son ki, yana son ki, kuma yannayin jikinki ba shine zai sa ya tsane ki ba dan ya auri wace ta fi ki yannayin jiki da wani abin da kike gannin zai iya zame maki cikas a zamantakewar ki da mijinki sai idan kin yarda , kema macece, komai yannayin jikinki kina da damar jan ragamarsa abinki, kin san waye mijinki, a tunanina zaki yi iya yinki ne dan gannin kin samu fuskar mijinki ta hanyar biyayya da tsaftatacen kishi ba banzan kishi ba, Haba Yumnah sai kace ba mace ba?" Akilah ta kuma fada a sanyaye sannan ta dora da fadin" Yumnah Mama bata da lafiya, bata da lafiya Yumnah, abinda ya hanna Ni juyawa kennan, ta saka damuwarki a ranta fiye da ke din, kima kwaso abu kina fada mata tana nisawa dan bata da yadda zata yi domin dad ya sharanda mata manyan sharudan da ba zata iya takawa ba, dan kuwa komai dadin gidansu ina mai tabbatar maki nan gidan mijinta nan ne kwonciyar hankalinta, kuma du irin abin nan dake faruwa Yumnah Mama zata fi kowa farin cikin ace kina dakinki a tsugunne irin kowace mace, kawai dai ita bata iya tankwasa zuciyarta a kanki ne, tana maki kallon yar jaririyarta ne, Yumnah a duk lokacin da kika yi kiranta kika fashe da kuka zata dafe kirji ne, tun tana boyewa har ya zamana bata iya yakin hakan dan kuwa jinninta hawa yake yi, kuma a abinda bata da maganinsa, Yumnah shin zaki so ace kece sanadiyar kamuwar mahaifiyarmu da mugun cuta a kan abinda fadan son kai ne kike yi ba na gaskiya ba?, Yau da ace mijinki na anfani da damarsa wajen wulakantaki ne , da ki sani Ni din nan sai na kwatar maki yancin ki, Yumnah da gatanki gaba da baya sai dai ki sani daga Abanmu har Ni yayarku ba zamu hau kan turbar karya ba dan jin dadinki, domin a duniya ake iya neman yafiya , a lahira sai dai a amshi sakamako gashi babu wanda ya san ranar mutuwarsa, kana biki budiri sai dai a wayi gari ka ji kanka a cikin kasa ba gaba ba baya!" Akilah ta karashe a tausashe tana share nata hawayen, dan bata san yaya zata yi da kanwar nata ba, bata son halin nan, tana yi mata uzuri ne dan har yanzu da yarinta a tare da Yumnah, sai dai zata so ta gane shi fa namiji zaka ji dadinsa ne idan kana kyautata masa, in kana wulakantashi komai son da yake maka komai kyanka komai takamarka tsaf zai watsar da kai kuma babu wanda ya isa ya dawo maka da shi sai Allah sai dai a ci da hakuri ko a rabu idan ba za'a iya ba, ita kuma bata yiwa kanwar Tata fatan zawarci , ta fita daga hannun TAUFEEK ta fada wani hannu? Da wahala ta auri saurayi mai mace daya, a halayanta ko mai mace dayan ta aura da wahala su jitu dan kuwa bata iya bambance duniyar mutane da ta ALJANU ba! Yumnah, gaba daya jikinta ya yi wani irin sanyi, a jikin kofar da take zaune na dakinta a hankali ta jinginar da kanta a jikin kofar Sosai maganar da suke tataunawa da yayarta yau ke neman yin mugun tasiri a zuciyarta Bambancin yayarta da mahaifiyarta shine, ita Mamanta ko me ta nuna tana so zata dafa mata baya ne, har kwanan gobe, yayarta kuwa idan ta kawo rigimarta sai ta duba in abin yi ne a yi in ba na yi bane fakat take nuna kin amincewar ta, shi yasa suke da dan rashin jituwa a tsakaninsu, dan ita gani take yi bata sonta ne, Ama a yau sai take ji kamar idan ta bi shawarar yayar Tata zata samu mafitar abinda yake damunta "Yaya zan yi ne? Yaya zan yi na iya kauda kaina a kansa? Yaya zan yi ya so Ni fiye da kowace mace?, Ta yaya za'a yi ya iya min so daya tak da babu Mahadi?" Yumnah ta fada a sanyaye tana rike kanta dake sara mata, a daidai lokacin ne TAUFEEK ya sauke ajiyar zuciya a hankali ya juya ya nufi dakinsa zuciyarsa cike da tausayinta da kuma jin eh lalle ko dan yayarta zai ci gaba da Binta a hankali har ta gane su zauna lafiya A hankali ya rintse idannuwansa sakamakon wani hasashe da ya yi a zuciyarsa Ba komai bane sai tunani da ya yi , ace Khausar ce ta auri waninsa.....eh lalle da ciwo , dole zai yiwa Yumna uzuri ya kuma nuna mata so Mikewa ya yi dan nufar bayi, a hankali ya yi murmushi yana tuna cewar wai tana tunanin ba zai iya dubanta ba dan Khausar ta fita sittin saba'in? Uhum mata kennan, zai so kwarai ta kwontar da hankalinta, kuma zai raba masu gida ne domin shi da kansa zai so kowace ta samu sakewa a gidanta, ama idan har Allah ya bashi ya'ya masu yawa zuwa gaba zai hade su ko ya haɗa zumunci mai karfi ta hanyar kawo ya'yan wannan wa wannan , shi kam baima san yaya zai dauki lamarin nan ba, zai fi bada karfi wajen fadawa ALLAH har ya samu daidaito a lamarin A bangaren Yumnah kuwa yayarta ci gaba ta yi da kwontar mata da hankali, ta hanyar nuna mata idan har tana son kwonciyar hankali to ta ringa sowa yar uwarta abinda ta sowa kanta, ta kuma daina dagawa mahaifiyarta hankali a kan abin son zuciya, idan har da cutarwa ta fada mata itace zata tayata yaki ba kowa ba! ( Dan uwa kennan, mai dadi, Allah ya karra lafiya my second mum💓😍😍😍😍😍😍😍).. Bai tashi nufar dakin Khausar ba sai da dare ya tsala sosai, a lokacin yana kyautata zaton ta jima da yin barci ma dan da ya fito asibiti ya juya kiran gagawa sakamakon wani aiki da ya yi kuma mutumen bai farka ba har lokacin da ake tunanin zai farka din ya wuce sosai, shine ya koma ya duba shi ya sake daukan wasu awannin dan duba shi idan bai farka ba kuwa sai addu'a kawai! A gajiye, zuciya cike da bege, da rauni mai karfin gaske ya karasa saman gadon da take kwonce idannuwanta lumshe tana barci hankalinta kwonce A hankali ya kwonta gefenta yana kallon fuskarta, a zuciyarsa kuwa yana tunanin to ita dazu fushi ne ta yi ko mene?...... [8/2, 7:47 PM] +234 708 653 0343: 💔💔💔💔❤‍🩹❤‍🩹💔💔💔💔 *DA CIWO A ZUCIYATA* 💔💔💔💔❤‍🩹❤‍🩹💔💔💔💔 _MALLAKIN_ *SAJIDA NIJAR* *FREE BOOK NE* 5️⃣9️⃣ *GARABASA, GARABASA, PROMOTION, PROMOTION DIN LITATAFAN MARUBUCIYAR A KAN FARASHI MAI SAUKI 1K, YAN NIJAR KUWA 1000 FRANCS CEFA* 1: Duk karyar kada 2: Yar mahaukaciya 3: Neman na kaina 4: Bani da zabi 5: Bak'a ce 6: Kutkale 7: Makauniya ce 8: Mage 9: Duk nisan jifa 10: Idan ka raina inda kake 11: Dutse 12: Alkalamin kadarata 13: Bani da zabi 14: Dakika Biyar 15:Wata kokowar 16: Aure yakin mata 17: Ni zan ladabi 18: Daga tafia daukar soja *Dukansu a kan farashi mai sauki, zaka saka dubu guda ne domin promotion ne nake yi, ka tuntubeni kan layina kamar haka +227 93 81 16 18, Sajida Nijar* Now *Da CIWO A ZUCIYATA* *Tallah, tallah, tallah* *SECRET DE LA FEMME DU MANGA* _Gidan Kamshi, Sirrin Manyan Mata, nesa tazo kusa,Amarya ,Uwar gida,Ango da mai gida Har ma da yan mata da samari shin kuna sane da cewa HAJIYA FUSAM ta shirya tsaf domin gwangwaje ku da turarakunta masu dankaran kamshi? Tare Kayan gyaram jiki na musamman ,wanda daga nesa kamshin ki kadai ya wadatar ya isar da sakon zuwanki waje,gidan ki kuwa sai ya zam abun kwatance wajen kamshi, kar na cika ku da surutu bara in fara zayyano su_ Farar Humura Bakar Humura Humura special, humura de bain Humura epicé Lait de nuit Parfums désodorisant Parfums rideau et dras Lait de nuit Alkam Kulakcam *Waɗannan kadan ne daga bangaren turaran ruwa* Gagab, sandal flex, Durot, durus, sandal fleur, tafarce, farce, sandal bangui, sandal, hypotonic sandal, al'ut, coktail creation VIP, Gajiji, Mankaji, turaran wutar labule da cafet, Aba malan, boulettes *Munada bangaren gyaran jiki kamar haka:* mai mai saka santsin jiki, mai mai kanshi, Kayan gyaran jiki mai saka fata ta yi santsi da laushi, kayan gyaran jiki mai saka fata ta yi fari, Sabulu mai saka fata ta yi haske, sabulu mai saka fata ta yi santsi, sabulu mai goge yanayin fata, mai wanda baya saka fari mai gyara fata Sayen na gari mai da kudi gida,sai an gwada akan san na kwarai💃💃 Hajiya Fusam na zaune a kasar Niger domin yin magana da ita kai tsaye tuntuɓi wannan number 97 82 44 94 *SECRET DE LA FEMME DU MANGA* Gidan Kamshi, Sirrin Manyan Mata💃💃💃💃💃 Tallah 3 Hajiata, ke kin san rayuwar aure sai da anini, in babu jagab a babar eriya oga ya kama tofa yawu da neman yadda zai yi bawan Allah, idan kuma babar haja a bude ham ai ba labari oga sai dai ya shiga ya fito kamar ya shiga kofar ruwa😔, zo ki ji, a farashi mai rahusa zaki gwangwaje ki rike bakin Elhaji gudun tada yara, ama idan lamari ya yi lamari tsaf zaku karya gado☹️🫣 🔥💥🔥💥🔥💥🔥💥🔥💥🔥💥🔥💥 *HOHOHO WANI KAYA SAI AMALE, DON JAKI BAZAI 'DAUKA BA, INA MATA MASU BUK'ATAR 'DAGA DARAJARSU A WAJAN MAZAJENSU INA MATAN DAKE SHAN WULAK'ANCIN MIJI KO NA KISHIYA ,INA MATAN DAKESON ZAMOWA MOWA AGIDAJEN AURENSU TO ALBISHINRU MAMAN ZARAH YAR MUTAN SOKOTO TA SHIRYA TSAF DOMIN GABATAR MAKU DA ZAFAFAN KAYAN MATA MASU KYAU DA INGANCI WANDA BASUDA ALGUS ACIKI , AKWAI MAGANI DANAYI BINCIKE AKANSU DAN FARIN CIKIN MA'AURATA NAMU BA IRIN NASU BANE KAYAN MU NA DABAN NE NA ASALIN SAKKWATAWAN SHEHU MASU ABUN MAMAKI* 07034251528 kayanmu masu inganci ne masu ladaftar da kowane irin namiji Kad'an daga cikin abubuwan da muke dasu Ingantaccen maganin nono , Wanda zai gyara maki nononki donmin dawo da martaban nononki acikin kankanin lokaci komai lalacewarshi kuwa sauran bayani sai mun had'u pc +234 703 425 1528 Maganin hips (hips up) Wanda zai ciko maki da hips dinki su cika suyi bul bul ga laushi dasu k'ara suyi dass abun sha'awar kowane namiji Maganin infection Sha yanzu magani yanzu Yana fatattakar sanyi cikin kankanin lokaci magani ne na maza da Mata insha Allah kowane irin sanyi gareki kikayi amfani dasu anwuce wajan Ingantacce Kuma sahihin maganin k'iba Wanda Zaki ciko acik kankanin lokaci zakiyi kibar ki Yar dai dai misali ki huta Zama da Rama Baki rasa ci ba Baki rasa sha ba amma kullum Ana kallon cewa kinada matsala agidan aurenki saboda wannan ramar , Rama batayi ba Sam Yar uwa Sabulun wanka Kalolin sabulun tsarki Turaren tsugunno Turaren al'ajab Hatsabibin turare Da sauransu 07034251528 Kalolin gumba Gumbar Dabino Gumbar gero Gumbar madara Gumbar matsi Gumbar ukku bala'i Gumbar tada zaune tsaye Gumbar sabon budurci Gumbar sa buzu kuwa Gumbar aya da kwakwa Gumbar ridi Gumbar mazari Sarauniyar gumba 3in1 Da sauran kalolin da bansamu fadi ba, Kalolin gari Garin mallaka Garin hutar da malaminki dakan jaraba Dakan Amare Dakan Ni'ima Dakan kishiya in bakiyi bani waje Garin sa buzu kuwa Garin buje.sharkaf Garin Dan la'asar Yayan hadiya mai suna dan la'asar Original Dan goshi Original Dan goshi (sabon salo) Original man damo Original man ayu Kitsen damo Sirrin tafin kafa Sirrin farinjini na uwargida da amarya harma da yan mata Kwallin idonka idona Muna hada set na sirrin mallaka hajiya ba boka ba Mallam sai tarin sirrika kema kizama kowa agidan surenki Akwai hadin sabon budurci ga yarinyar data rasa budurcinta ta hanyar fyade ko yaudarar d'a namiji da izinin Allah akayi maki wannan hadin to an wuce wajan sauaran bayani sai mun had'u pc Kalolin tsumi Tsumin mallaka Tsumin jaraba Tsumin madarar ni'ima Tsumin tabaje Tsumin Amare Tsumin sabon budurci Tsumin nono rakumi Matan gaske Ruwan jaraba, Da sauran kalolin da ban fada ba Kalolin matsi da basuda illa ajikin mace sai dai ma sukara maki lafiyar Matsin Dan mannau Matsin mallaka Dan la'asar Sabon budurci Mak'alemata Mashahurin matsi Ukku bala'i Matsin uban budurwa Akwai gumba ta matsi wadda Shanta akeyi ga matan da basa son yin matsi Muna hada set ga wadda Allah ya jaranfa da matsalar fyade har yarasa budurcinta , muna hada mata kaya ingantattun don dawo da martabar ta, Hohohohoho in ana dara fidda uwa ake *Kyallen al'ajabi* babban sirrin mallaka mai abun al'ajabi mallaki naki don samun damar shiga cikin jerin mata masu fada aji a gidan mazajensu , KARKU manta da sunan maman zarah sokoto sayen nagari maida kudi gida 07034251528 ina maraba daku sayen daya ko sari ina Sokoto sannan ina aikawa kowane gari cikin aminci da yardar Allah Ga Wanda suke bukatar ganin kalolin kayana to suyi sarving number na suyimun magana nayi sarving number ku zaku dinga ganin kalolin kayana a status ngd sosai 07034251528 Maman zarah mabera SOKOTO A hankali ya shiga zagaye fuskarta da yar yatsarsa yana kallon reaction dinta Murmushi ya yi gannin sai zumbura baki take yi, karshema ta bude idannuwan tana ganninsa ta idasa yin takwaf takwas da fuskarta ta fashe da kukan da sam bai zaci ganninsa daga idannuwanta ba Tashi daya zuciyarsa ne ta shiga bugawa , ya Allah, kar dai duka wannan din bacin ran yace sai ta cike kwanakin da ta san sarai yana da saura tare da ita ne? A hankali ya ji zuciyarsa na neman rufewa da wani rauni, shin shima zai kuma dasa wani sabon jinyar zuciya ne bayan ya jima yana ciki? Shin zai ringa wahalar son wace ba zata bashi kulawa ba? Ya Allah mene hakan kuma? "Kukan bakya son ganina a gefenki ne Khausar?" Ya furta cen kasan makoshi yana jin zuciyarsa na dokawa da karfin gaske A hankali Khausar ta juyo tana facing dinsa, what? Kukan bata son ganninsa yake magana? Lalle TAUFEEK, idan ta ki son ganninsa ta so gannin wa a duniyar ta? A hankali ta kalli rikon da ya yiwa hannayenta a kwoncen da suke yana kallonta ya ce" Me yasa kike kuka? In tashi in tafi bakya so na zo?" Khausar ta turo baki tana yin yannayin tamkar yar karamar yarinya A hankali ta ce" Ni ba kukan wannan nake ba" "To menene? Baki da lafiya ne?" Ya fada a dan gagauce Khausar ta zubawa fuskarsa ido, a hankali ta ce" Taufeek, aikina fa? Ka cema Hajia wai ba inda zan je, kuma ka ga na jima ban je ba, dan Allah TAUFEEK kar ka rabani da aikina, " A bayane ya sauke ajiyar zuciya, da gaya ya dan tsareta da ido ya ce" To ki yi zamanki mana ba sai in ringa maki albashinki kina gida ba?" A hankali Khausar ta girgiza kai ta ce" TAUFEEK ka fa san ina son aikina, kai shaida ne na irin yadda na kashe kaina na yi karatu, kuma kai shaida ne ina son aikin nan ko?" Kai ya gyada yana kallonta Khausar ta jimke hannayensa a hankali ta ce" idan ka rabani da aikin nan yaya zan yi? Ina iya yin kuka daga safe har dare fa, kuma zan daina cin abinci kwata kwata" Ido ya zarro a hankali ya ce" Kin tabata? Cikin nan zai iya jurewa?" Khausar ta ture hannunsa tana turo baki ta ce" Sai a masa dole ai , kuma in hau cen karshen karfen cen in fado in fashe!" TAUFEEK ya idasa zarro idannuwan yana sakin dariya ya sake kallon karfen ya kalleta a hankali ya janyota jikinsa ya rungume sosai kasa kasa ya ce" Idan kika fashe Ni kuma in shiga ina?" Khausar ta lumshe idannuwanta tana jin hannunsa na kokarin yawo a cikin rigarta, a hankali ta bude idannuwanta suka yi ido hudu kasa kasa ta ce" TAUFEEK washhhhh " Tsigar jikinsa ta tashi d sauri ya sake matse mata waje muryarsa a shake ya ce" Khausar Please, i nd U" Idannuwan ta mayar ta rufe tsoro na riskar kirjinta ama kuma ta ki hannashi, a hankali ta ce" Aikin nawa fa?" TAUFEEK da ya fara yin nisa da kyar ya iya cewa" Zaki koma " Khausar ta sauke ajiyar zuciya tana jinsa kamar zai haukata mata jiki A hankali ta sake furta" TAUFEEK ina so in ga Abana kuma" TAUFEEK ya dago rinanun idannuwansa yana kallonta a hankali ya hade bakinsa da nata sannan ya koma daga barin da zai fi jin dadin sarrafa ta Wato a jiya sharar fage zan ce ya yi mata? Ko kuwa dan ya ga har ta iya kula da kanta da kanta ne? A yau dai ainahin maza a yau Khausar ta ji maza, domin tun tana kokari irin nata sai da ta fara fita a hayacinta jikinta ya nemi saki , hawaye kuwa wani ke kokar wani Tana ji tana gani ya kaita bayi , ko daga hannunta bata iya yi da kyau , idannuwanta kuwa har sun sundume dan azabar da ta sha A yau ne ta samu ainahin gashi irin na yan mata domin sai da ya tara ruwan ya sakata sannan ya koma ya cenza shinfidar gadon dan ba zai kwontu ba, lalle jikawar ta jiku matar jikan Hajia Da kyar ta iya rukunkume jikinta jin yana sake shafar hannayenta A hankali ta rintse idannuwanta muryarta bata fita da kyau ta ce" Kasheni zaka yi? Ka karani fa" Murmushi ya yi yana ta lumshe ido, shi kam da zai samu kari babu abinda zai hannashi sake wanke goma ya dangwala biyar Sosai jikinta ya idasa rikicewa da zafi da kuma zafin ciwon haka da ta sha Duk yadda ta so karfafa jikinta bayan fitarsa da safe ta mike gazawa ta yi domin ko sallah sai da ya taimaka mata ta yi kuma ya bata magani har sau biyu ama zafin zazzabin ya ki sauka Kusan karfe takwas sai gashi dauke da ledar magani da kuma flask din abinci Sai da ya matsa mata ta dan taba sannan ya jonna mata karin ruwa ya zauna yana dan shafa gashin kanta har ta yi barci sannan ya fita ya ja mata kofar ya sauka ya nufi bangaren abansa dake nemansa zuciyarsa cike da tausayinta, gaskiya ya mata zuwa ne na gaske baiwar Allah ashe zata iya raunata haka Zama ya yi nesa da Hajia dan ba wani son surutu yake yi da safiyar nan ba Mikewa ta yi ta dawo daf da shi ta zauna kasa kasa ta ce" Ina kwana magidanci?" Kallonta ya yi ya mata shiru , Abansa kuwa ya sakar masa harara dan sarai ya ji Hajia ce ke gaishe shi ya ki amsawa Murmushi ya yi yana sosa keya ya ce" lfy kalu" Mama ta kalle shi a zabure, tana mamakin amsawa ne ya yi? Kai jama'a shin yaya zata yi da rikicin TAUFEEK da kakarsa? Aba ya yi kwafa ya ce" Zaka yi bayani ne Elhaji karami, nace zaka yi bayani ne!" Hajia ta kalli Aba ta ce" To fa, daga zuwansa me ya maka kuma?" Mama ta kalli Hajia da mamaki ta ce" Hajia kece zaki gaishe shi ya wani amsa ko kunya baya ji?" Hajia ta kama haba tana kallonsu, sai kuma ta maida kanta kan TAUFEEK ta ce" Shi yasa nake maka maganin baki, kai fa farin jinin ka mai kwanonina da matarsa sun saka maka ido, wato bakinmu ake kallo a ga me muka ce, ta Allah ba ta mutun ba jikana ya fi karfin yawan maganar yan uba!" Daga maman har aba suka kalli junna, Mama ta soke kai Aba kuwa mai zai yi banda murmushi Ya gyada kai yana al'ajabin mahaifiyarsa A hankali ya ce" Uhum, Yaya maganar tafiyar ne?" TAUFEEK ya dago ya kalli Aba, sai kuma ya kalli Hajia, kasa kasa ya ce" Ba nace maki ba zamu tafi ba wannan shekarar?" Hajiarma kasa kasa ta ce" to in na mutu kafin badin fa?" TAUFEEK ya harareta a fakaice dan ƴaƴanta na nan ai, a hankali ya ce" Na fada maki ai da saura mutuwar in sha Allah, kuma Khausar fa bata da lafiya yaya zan tafi nan da yan kwanaki in barta? " Hajia ta washe baki tana zarro ido ta ce" Kai haba, shafa min fada min ya faru ne?" TAUFEEK ya tsareta da duban mamaki, kasa kasan nan ya ce" Me ya faru?" Hajia ta zabga masa harara ta ce" Bafa na son wulakanci ka ji na fada maka!" Shima ya daure fuska ya ce" Ni dai ki rabani da su, ke da zamu je yawon gannin turawa da ke? Abinda ga umura na zuwa ba sai mu je ba? Haba tawan" Hajia ta yi shiru tana nazari, sai kuma ta kalli su Aba dake kallonsu kowane na so sai ya ji me suke tataunawa ama basa ji dan magana ce kamar ta munafunci rada rada Sai da ta wani ci magani ta ce" Ni mai kwanoni zuwana hajin nan nawa?" Aba ta kalli Hajia, shi yaya zai yi ya iya irgawa abinda tun mahaifinsa da rai ake zuwa ? Da ladabi ya ce" Hajia ai an jima ana zuwa alhamdulilah" Hajia ta ce" Masha ALLAH, wani abinma ai sai ya zama kamar barna, kudin bana a ciyar da marayu badi ma je Ni da Magidanci dan ba zaka hadani da matanka su batar da Ni Ko su buden tagar jirgi na fado ba, bale ita wannan tana kallo sai su zane Ni bata da karfi ko kadan bale ta kwaceni!" Aba ya kalli TAUFEEK da kallo irin mai tafe da gargadin nan TAUFEEK ya sada kai yana kikifta ido Aba ya sauke ajiyar zuciya ya ce" to Hajia shikenan Allah ya saka da alkhairi ya bada kadan niya" Hajia ta ce" Amen" TAUFEEK ya sauke ajiyar zuciya ya kalli mahaifinsa ya ce" Aba, dama ina so na maka maganar su Yumnah ne, ina son raba masu gida idan har ba damuwa in sha Allah" Hajia ta yi turus tana kallonsa , ta kalli Aba tana kikifta ido , sosai ta so kamewa ta ki shiga ama ta kasa ta ce" Yo a kan wace masifa, Allah na tuba ubaanka ba su uku ne a jere ba! A kan me zaka raba masu muhalli?" TAUFEEK ya zuba mata ido, kasa kasa ya ce" Tashi ki bar nan kin ga ba da ke nake ba" Hajia ta ja tsaki tana mikewa ta koma daf da Mama ta ce" Aikin banza kai babu fa yar da ta isa ta juyan jika ina raye, a kan wani shegen dalili zaka wara iyalinka iyi? Ni kuma a kaini wani gidan to? Aikin banza kawai!" Aba ya rasa ta inda zai fara, mama kam dama ba cika tofawa ta yi ba idan ana irin haka, sai ya zamana Hajia da TAUFEEK sunna kallon junna ne kowa da abinda ke ransa TAUFEEK ya gyara zama a ladafce ya ce" Ku ji, kunna ji? Saura kiris🤗😂 💔💔💔💔❤‍🩹❤‍🩹💔💔💔💔 *DA CIWO A ZUCIYATA* 💔💔💔💔❤‍🩹❤‍🩹💔💔💔💔 _MALLAKIN_ *SAJIDA NIJAR* *FREE BOOK NE* 6️⃣0️⃣ *GARABASA, GARABASA, PROMOTION, PROMOTION DIN LITATAFAN MARUBUCIYAR A KAN FARASHI MAI SAUKI 1K, YAN NIJAR KUWA 1000 FRANCS CEFA* 1: Duk karyar kada 2: Yar mahaukaciya 3: Neman na kaina 4: Bani da zabi 5: Bak'a ce 6: Kutkale 7: Makauniya ce 8: Mage 9: Duk nisan jifa 10: Idan ka raina inda kake 11: Dutse 12: Alkalamin kadarata 13: Bani da zabi 14: Dakika Biyar 15:Wata kokowar 16: Aure yakin mata 17: Ni zan ladabi 18: Daga tafia daukar soja *Dukansu a kan farashi mai sauki, zaka saka dubu guda ne domin promotion ne nake yi, ka tuntubeni kan layina kamar haka +227 93 81 16 18, Sajida Nijar* Now *Da CIWO A ZUCIYATA* *Tallah, tallah, tallah* *SECRET DE LA FEMME DU MANGA* _Gidan Kamshi, Sirrin Manyan Mata, nesa tazo kusa,Amarya ,Uwar gida,Ango da mai gida Har ma da yan mata da samari shin kuna sane da cewa HAJIYA FUSAM ta shirya tsaf domin gwangwaje ku da turarakunta masu dankaran kamshi? Tare Kayan gyaram jiki na musamman ,wanda daga nesa kamshin ki kadai ya wadatar ya isar da sakon zuwanki waje,gidan ki kuwa sai ya zam abun kwatance wajen kamshi, kar na cika ku da surutu bara in fara zayyano su_ Farar Humura Bakar Humura Humura special, humura de bain Humura epicé Lait de nuit Parfums désodorisant Parfums rideau et dras Lait de nuit Alkam Kulakcam *Waɗannan kadan ne daga bangaren turaran ruwa* Gagab, sandal flex, Durot, durus, sandal fleur, tafarce, farce, sandal bangui, sandal, hypotonic sandal, al'ut, coktail creation VIP, Gajiji, Mankaji, turaran wutar labule da cafet, Aba malan, boulettes *Munada bangaren gyaran jiki kamar haka:* mai mai saka santsin jiki, mai mai kanshi, Kayan gyaran jiki mai saka fata ta yi santsi da laushi, kayan gyaran jiki mai saka fata ta yi fari, Sabulu mai saka fata ta yi haske, sabulu mai saka fata ta yi santsi, sabulu mai goge yanayin fata, mai wanda baya saka fari mai gyara fata Sayen na gari mai da kudi gida,sai an gwada akan san na kwarai💃💃 Hajiya Fusam na zaune a kasar Niger domin yin magana da ita kai tsaye tuntuɓi wannan number 97 82 44 94 *SECRET DE LA FEMME DU MANGA* Gidan Kamshi, Sirrin Manyan Mata💃💃💃💃💃 Tallah 3 Hajiata, ke kin san rayuwar aure sai da anini, in babu jagab a babar eriya oga ya kama tofa yawu da neman yadda zai yi bawan Allah, idan kuma babar haja a bude ham ai ba labari oga sai dai ya shiga ya fito kamar ya shiga kofar ruwa😔, zo ki ji, a farashi mai rahusa zaki gwangwaje ki rike bakin Elhaji gudun tada yara, ama idan lamari ya yi lamari tsaf zaku karya gado☹️🫣 🔥💥🔥💥🔥💥🔥💥🔥💥🔥💥🔥💥 *HOHOHO WANI KAYA SAI AMALE, DON JAKI BAZAI 'DAUKA BA, INA MATA MASU BUK'ATAR 'DAGA DARAJARSU A WAJAN MAZAJENSU INA MATAN DAKE SHAN WULAK'ANCIN MIJI KO NA KISHIYA ,INA MATAN DAKESON ZAMOWA MOWA AGIDAJEN AURENSU TO ALBISHINRU MAMAN ZARAH YAR MUTAN SOKOTO TA SHIRYA TSAF DOMIN GABATAR MAKU DA ZAFAFAN KAYAN MATA MASU KYAU DA INGANCI WANDA BASUDA ALGUS ACIKI , AKWAI MAGANI DANAYI BINCIKE AKANSU DAN FARIN CIKIN MA'AURATA NAMU BA IRIN NASU BANE KAYAN MU NA DABAN NE NA ASALIN SAKKWATAWAN SHEHU MASU ABUN MAMAKI* 07034251528 kayanmu masu inganci ne masu ladaftar da kowane irin namiji Kad'an daga cikin abubuwan da muke dasu Ingantaccen maganin nono , Wanda zai gyara maki nononki donmin dawo da martaban nononki acikin kankanin lokaci komai lalacewarshi kuwa sauran bayani sai mun had'u pc +234 703 425 1528 Maganin hips (hips up) Wanda zai ciko maki da hips dinki su cika suyi bul bul ga laushi dasu k'ara suyi dass abun sha'awar kowane namiji Maganin infection Sha yanzu magani yanzu Yana fatattakar sanyi cikin kankanin lokaci magani ne na maza da Mata insha Allah kowane irin sanyi gareki kikayi amfani dasu anwuce wajan Ingantacce Kuma sahihin maganin k'iba Wanda Zaki ciko acik kankanin lokaci zakiyi kibar ki Yar dai dai misali ki huta Zama da Rama Baki rasa ci ba Baki rasa sha ba amma kullum Ana kallon cewa kinada matsala agidan aurenki saboda wannan ramar , Rama batayi ba Sam Yar uwa Sabulun wanka Kalolin sabulun tsarki Turaren tsugunno Turaren al'ajab Hatsabibin turare Da sauransu 07034251528 Kalolin gumba Gumbar Dabino Gumbar gero Gumbar madara Gumbar matsi Gumbar ukku bala'i Gumbar tada zaune tsaye Gumbar sabon budurci Gumbar sa buzu kuwa Gumbar aya da kwakwa Gumbar ridi Gumbar mazari Sarauniyar gumba 3in1 Da sauran kalolin da bansamu fadi ba, Kalolin gari Garin mallaka Garin hutar da malaminki dakan jaraba Dakan Amare Dakan Ni'ima Dakan kishiya in bakiyi bani waje Garin sa buzu kuwa Garin buje.sharkaf Garin Dan la'asar Yayan hadiya mai suna dan la'asar Original Dan goshi Original Dan goshi (sabon salo) Original man damo Original man ayu Kitsen damo Sirrin tafin kafa Sirrin farinjini na uwargida da amarya harma da yan mata Kwallin idonka idona Muna hada set na sirrin mallaka hajiya ba boka ba Mallam sai tarin sirrika kema kizama kowa agidan surenki Akwai hadin sabon budurci ga yarinyar data rasa budurcinta ta hanyar fyade ko yaudarar d'a namiji da izinin Allah akayi maki wannan hadin to an wuce wajan sauaran bayani sai mun had'u pc Kalolin tsumi Tsumin mallaka Tsumin jaraba Tsumin madarar ni'ima Tsumin tabaje Tsumin Amare Tsumin sabon budurci Tsumin nono rakumi Matan gaske Ruwan jaraba, Da sauran kalolin da ban fada ba Kalolin matsi da basuda illa ajikin mace sai dai ma sukara maki lafiyar Matsin Dan mannau Matsin mallaka Dan la'asar Sabon budurci Mak'alemata Mashahurin matsi Ukku bala'i Matsin uban budurwa Akwai gumba ta matsi wadda Shanta akeyi ga matan da basa son yin matsi Muna hada set ga wadda Allah ya jaranfa da matsalar fyade har yarasa budurcinta , muna hada mata kaya ingantattun don dawo da martabar ta, Hohohohoho in ana dara fidda uwa ake *Kyallen al'ajabi* babban sirrin mallaka mai abun al'ajabi mallaki naki don samun damar shiga cikin jerin mata masu fada aji a gidan mazajensu , KARKU manta da sunan maman zarah sokoto sayen nagari maida kudi gida 07034251528 ina maraba daku sayen daya ko sari ina Sokoto sannan ina aikawa kowane gari cikin aminci da yardar Allah Ga Wanda suke bukatar ganin kalolin kayana to suyi sarving number na suyimun magana nayi sarving number ku zaku dinga ganin kalolin kayana a status ngd sosai 07034251528 Maman zarah mabera SOKOTO TAUFEEK ya gyara zama, a ladafce ya ce" Aba dama na kula akoy takura a zaman ne nake cewa ita Khausar din a kaita wancen gidan ma shigowar gari ita kuma Yumnah sai ta zauna a nan din idan har ba damuwa?" Hajia ta zuba masa ido, sai kawai ta zauna daf da Mama ta shiga magana kwallah na taruwa a idannuwanta ta ce" yanzu daukanta zaka yi ka kaita nesa da Ni bayan na san in dai tana cen kana cen ne? Inma daukewar zaka yi ka ɗauke ita yamar mana a bar min ita KHausarar? Haba magidanci ko laifi na maka ai sai ka sanar min in baka hakuri ko?, " Dubansa ya maida kanta, kasa kasa ya ce" Na ce zan tafi in barki ne? Me yasa kike son rigima?" Hajia ta kikifta ido tana share yar kwalarta ta ce" Ahyo sai ka yi bayani da Yaren da zan gane , sai kace zaka dauke Hajia da khausara ba wai Khausara kadai ba ko?" Baba da mamaki ya gama kashe shi yana kallon Hajia da TAUFEEK ya ce" A'a, ya dauke ki fa Hajia? Ni fa?" Hajia ta zuba masa ido kafin ta dafe haba ta mike tsaf ta koma gefen TAUFEEK ta riko hannunsa tana kallon baba da mama shekeke ta ce" Haka kawai iyayen wane kakanin wane zaka ce wani kai fa, yo goyaka zan yi ko me zan maka fisabililahi, yaro zan bari shi kadai ya je nesa da zama duniya cike da makiyansa in saka ka a gaba nai maka wata tsiyar? Gaskiya ka cenza tunani dan wannan din sam ba tunanin mutanen kirki bane, Ni kam ka ga tafiyata bari in je in yiwa Khausarar dumame an ceba lafiya ta yiwu baiwar Allah ta jigatu, ga jiki irin na ya'yan hutu jikin nan na Khuausar ba wata wahala ya sani ba fa, ka daina ganninta haka kadan zai iya rikitata bale da yawa Allah dai ya sa magidanci bai yi aiki na son rai ba!" Ta fada ne tana neman hijabinta ta zumbula ta yi gaba tamkar zai tadeta ta fadi Kansa a kasa yake tunda ta fara bayanin ta, bai iya dagowa ba dan tsabar jin kunya da nauyin maganar kakarsa har ta bar wajen da kamar mintuna biyar shiru ne a wajen, dan kuwa ya gama tsarguwa da kansa ne , Hajia ta gama watsa shi a gaban iyayensa bayan bakinsa da nata basu yi maganar ya taba Khausar ba, wannan wani irin neman magana ne "Kana ji?" Aba ya fada shima bayan ya yi yaki da nasa jin nauyin da kyar , dan kuwa a bayanin mahaifiyarsa ba boyewa cewar wani abu ya shiga tsakaninsu da matarsa ne, dan mama Hajiar na tafia ta yi ciki tana kaye kayen abubuwan da ba'a sakata ba Da kyar ya dan iya dagowa Baba ya ce" babu fa maganar ka ɗauke min uwata gaskiya, kiri kiri ka kwacen uwa, kuma Allah ya hada jinninta da Khausar, so ka zaba ko ka tada wani ginnin daga cen wajen Khausar din ta koma, ko kuma ka maida Yumnah din wani gidan idan har hakan ya zama dole, dan gaskiya babu inda zaka kai min uwa tunda ba gidanka zan ringa zuwa ina zama ba ko?" TAUFEEK ya gyada kai cike da jin kunya, Baba ya mike yana daukan hularsa ya ce" Bari in leka gidan malam Anas in yi zumunci" TAUFEEK ya ce" A dawo lafiya" Mama dake ciki ta fito da dan sauri tana miko masa wayarsa ta ce" Allah ya tsare" Daga haka aka bar Mama da TAUFEEK a falon TAUFEEK ya ja numfashi yana yin kwafa hadi da dane lebe ya ce" ina dalili mata ki matsa min, gaba daya Maman iyayen gidan nan bata jin magana!" Mama ta sake bude ido tana kallonsa ta ce" TAUFEEK uwar tamu ce bata jin magana?" TAUFEEK ya zubawa mama ido sai kumaa ya dan matso daf da ita ya ce" Yanzu dan Allah matar mai kwanoni kina ji kika kyale ta min ba dadi?" Mama ta kawo hannunta ta zungureshi da karfi tana sakar masa harara ta ce" Ka fa kiyayeni fa, ka fa kiyayeni, Tom, tashi Ni ka bani waje kuma na fada maka kawata ta kawo yaronta wai aikin da za'a masa jaka dari uku, gaskiya ka yi wani abu ba zai yiwu ba ko ka biya ko ka saka a litafina na asibitin" TAUFEEK ya yi murmushi ya ce" To in sha Allah an gama" Har ya mike mama ta yi kiransa ya dawo ya zauna A nutse mama ta ce" TAUFEEK, ina so in tunatar da kai, ko me kake yi ka kamanta adalci tsakanin iyalinka, ka ga a lokacin da ka zo min da maganar wai Khausar ta matsa maka ta dage sai ka auri Yumnah tunda tana sonka fisabililahi na yi maka tambayar au ita Khausar din ba soyaya ce kuke yi ba ka budi baki ka ce min a'a zumunci ne na fada maka cewar idan har da wani abu tsakaninka da Khausar ka yi gagawar tabattar da shi kar ka bari ta yiwa kanta gurbin wata a duniyar ka, ka nunan ba komai ai itacema ke son alakarka da Yumnah shi yasa zaka yi, to ka sani a yanzu babu maganar alfarmar wance , magana ce ta matanka, kowace nada haki a kanka, wanda idan ka tauye Allah zai kamaka da shi, ka kula ka rufawa kanka asiri ka fita hakinsu, nima na fi so ka raba din dan hadewar wani lokacin bata da wani fa'ida, sai a rayu a takure babu yadda za'a yi, ama in har da halin rabawar a ba kowace filinta ta yi rayuwarta da mijinta da tsarin gidanta ka ji?" TAUFEEK ya gyada kai yana tuna ranar nan da mamaki ya hanna shi sukuni dan tashi daya mahaifiyarsa ta nuna masa ta fa fi shi Sannin kansa, sai da ya jajirce ya kade mata wannan tunanin sannan ta kyale shi, ashe dai tana tune itama Sosai Mama ta masa nasihar da ta dace sannan ta sallame shi Sai da ya biya wajen hajia ya dauki abincin sai harararta yake ita kuwa ko a kwalar rigarta saima da ta hada tace su je ne ya dakatar da ita yace ba inda zata sannan ya yi tafiyarsa A falo ya ajiye abincin ya dauki plate mai kyau ya zubawa Khausar isashe ya je dakin nata ya ajiye mata domin barcinta take yi har yanzu , karin ruwan nema ya ci rabi, kawai wanda zata ji karfin jikinta ne dan har ga Allah ta wahala iya hawala Daga nan dakin Yumnah ya shiga ya fitar da ita suka sauko ya zauna ya sakata zuba masu abincin sannan ya sakata ci yana kallon tv hadi da dan jefo mata fira kadan kadan tana bashi amsa har suka gama ya bata damar komawa dakinta Sosai ta ji wata salama na sake shigarta a lokacin da ta koma dakinta, haka kuma a kasan zuciyarta tana jin zata iya jurewa in har bata gannin Khausar din! Sai da ya sake yin wanka ya koma dakin A hankali ya hau saman gadon da wayarta wace ya saka mata sim ya kunna ya ajiye gefenta kadan sannan ya shiga shafa gefen fuskarta yana kallonta har ta fara bude idannuwanta Rinanun idannuwanta ta sauke a saman tasa fuskar, a hankali ta rintse ido tuno irin wahalar da ta sha a hannunsa....ashe TAUFEEK baya tausayinta? Shine zai kasheta ko? Lalle Murmushi ya yi gannin yadda ta turo baki a hankali ya ce" Morning wifey" Khausar ta sake bude idannuwan nata tana kallonsa, sai kawai ta shagwabe fuska ta narke masa ta fara kukan shagwaba A hankali ya sakata jikinsa bayan ya cire nata karrin ruwan A hankali yake shafa bayanta kasa kasa ya ce" Na yi laifi, i'm sorry, ama kin ga zaki saba ai ko anmatana?" Ita dai ajiyar zuciya take saukewa kuma bata son matsewar wajen dan ta kula kamar yarensa na cenza salo ne daga rungume rungume, ita kuma a yadda take jinta in har ya sake gwada wani abin tsaf yake iya aikata summan da ba dawowa, ita dai a wannan abu bata tunanin za'a saba Allah ya taimaketa ba ita kadai gareshi ba, har ga Allah har ranta sai da ta ji tana tausayawa Yumnah, da kuma gannin kokarinta na rigima dan an kawo mata wace zata tayata raba wannan tashin hankali mai saka mace kuka( uhum ki dai saba sai ki ji kema Hajia Khausarar Aba) Kasa kasa TAUFEEK ya ce" Na kira maki Aba ne zaki daina kukan?" Da sauri ta dago tana kallonsa lokaci daya ta saki murmushi hadi da gyada kai ta ce" Eh, dan Allah ka kira min shi da kuma Mama da su Aisha da kuma rukaya, ka kaini na ga Abana *YAYANMU*" Dankari, wato yau bakin Khausar ne ke kiran TAUFEEK ƴaƴansu? Lalle TAUFEEK din Hajia ya yi aiki irin na rashin arziki , murmushi kawai ya yi bai barta ta gane ƴaƴansu ta kireshi ba ya danna numbar Aba ya miko mata a wayar Tata Wayar take kallo iphone ce dankareriya irin tasa ce wancen, bata san Tata bace itadai tunda ya zo da ita da daren nan ya barta a nan ta ajiye masa gaban sif A raunane Khausar ta amsa salamar da abanta ya yi mata, murya na rawa ta ce" Abana, shine kace zaka zo ama baka zo ba? Abana shine kace zaka kira baka kira ba, kuma kace ana yin kwana guda za'a kawo Ni har yanzu shiru, haka kuma Mama ko ta leko Ni, su Aisha ko su zo inda nake, hakama auta ko nemana baya yi?" Aba ya saki yar dariya yana kallon Mama dake tankade ya ce" yar gidan Aba duka wannan din laifin da na yi ne? To a yafewa Aba kin ji Khausar Aba, ya gida, ya yayanku da iyayenku yaya Hajia uwata?" Khuausar ta saki yar dariyar itama ta ce" Aba, kowa lafiya, sai dai Hajia ta yi rashin lafiya, ama ta warke yau dai ban lekata ba, Abana yaushe zaka zo?" Mama da ta dakatar da tankaden ya saki murmushi hadi da jin damuwarta ta ragu, dan har ga Allah tana cikin damuwar hakayar y'ar Tata, takan yi tunanin kar dai aje tana cen tana zuba shirme? A hankali ta ce " Abansu bani ita mana" Aba ya yi murmushi ya mikawa mama yana fadin" Khausar din? Bakya jin kunyar yau?" Mama dai ta kyale shi dan haka yake sakota a gaba wai tana kukan ta aurar da Khausar har a gaban auta yi mata yake yi wai ta kasa cin abinci tana tunanin yarta Mama na murmushi jin Khausar ta ce" Ina fatan kina zaune kalau da kowa? Bakya raina kowa kuma bakya halaya kamar na wace bata da wayo?" Khausar ta kalli TAUFEEK dake ta murmushi ta ce" Yayanmu wai ka ji mama ko?" Da Maman da TAUFEEK din a tare suka zarro ido, mama ta ce" Lah ila ha ilalahu ke Khausar!" Tana fada ta mikawa Aba wayar da sauri ta shige daki, Aban kuwa me zai yi banda dariya har dafe haba yake yi ya ce" Khausar ta buya ai maman naku kin san yanzu kunyar TAUFEEK take ji kamar sabon bakonta, bani shi mu gaisa" Itama Khausar din sai ta ji wani nauyi ga kuma kunya, dan har ga Allah da tace ya ga mama ta fada kamar yadda maman ke raba su rikicinsu a gida ne, yadda suka saba firarsu normal, sai yanzun da ta tuna yanzun fa miji yake a gareta sirikin Mama sai ta rufe fuskarta da hannayenta tana jinsa yana fira da Aba hankali kwonce har suka yi salama " Yana kashe kiran ya shiga wajen hoto ya dauketa hoto a yadda ta yin nan sannan ya karasa yana kallonta ya janyota jikinsa a hankali ya ce" Open your eys Baby" Khausar ta dan bude idannuwan tana zarowa jin ya ce mata baby Wata irin matsananciyar kunya ce ta kamata gannin yadda rigar nan ta mata, rigar ruwan hanta ce kuma mai santsi ce, ga wata tsaga da gareta wace ta fitar da cinyarta waje, da ta yi haka din nan hoton sai ya balakin kyau harda zanen kunshinta radau ga fara kal din hular dake kanta Sai dai hoton wani irin kunya da ya bata wace ta so wuce misali A hankali ya dago fuskarta da take boyewa kasa kasa ya ce" Na jima ina adu'ar ganninki a haka a matsayin halalina" Idannuwanta ta bude a hankali ta zuba su cikin nasa Ba jin kunya bale nauyi ya sake dubanta ido cikin ido kasa kasa ya ce" Na jima ina son ki yar Aba, na jima ina wahalar hakan " A hankali Khausar bayan ta boye fuskarta a kirjinsa ta ce" Me yasa ka ki sanar min? " Rungumeta ya yi a jikinsa kasa kasa ya ce" Kina tune bayan kin amince mu yi zumunci wani lokaci a kasan shukar aunty mai dambu muna cin dambu ake maganar wata da ta auri wani ko salif ko me, wanda shekara hudu ne ya bata , kina budar baki kika ce a duniya kina mamakin mata, sunna da wani tunani marar anfani, ke yaya za'a yi ki taba son yaro? Ko mai mace daya ke ya maki kadan sai tsoho gaskiya, idan kina tune na fara cin dambun kennan na mike na yi tafiyata ban shiga jarabawar da za'a yi ba har kika min fushi saboda haka, kina tune?" Da sauri Khausar ta dago tana kallonsa, ya Allah, kwarai an yi haka, a lokacin yar ajinsu ce ta auri saurayinta yake dukanta kuma kowa ya sani, ita da ta budi baki ta yi maganar nan ai kowa ra'ayinsa ne yake badawa a lokacin, kuma ita da ta fadi hakan gani take yi ne ina dalili mace ta tashi ta auri yaro har ya ringa dukanta? , Kasancewar ta tashi da yannayin jikin nan nata ne ita bata taɓa sakawa ranta zata auri saurayi ba, ko yaro ba, saima ta fi sha'awar gidan yawa a ganninta cen ne zata rayu ba tare da an wulakanta yannayinta ba A hankali tana kallonsa ta ce" Ina tune, ranar za'a yi mana jarabawa na yi ta kiranka da wayar abokinka ka kyale Ni, wanda da ka dawo ka ki nemana sai da na je na nemo ka, to ama me na yi Ni?" Harara ya sakar mata yana kama bakinta da yar yatsarsa ya ce" Bakin nan , shine ya ringa fadin yan kannanun magangannun da suke hadasa min hawan jini na bacin rai, sai in rasa ta inda zan fara, domin nakan samu kaina a cikin rikici biyu ne, bana so dalilin kasa rike abinda ke raina in zo in rasa ki, ba soyayar taki kuma ba zumuncin, ama ai na yi iya yina kin zama tawan Ni kadai " "Ya Allah" Khausar ta fada tana sake zuba masa ido A hankali ta ce" Shine ka kyaleni nake neman mijina ido rufe, idan na zo ina kukan ba'a sona sai ka wani ce kai ba kana so na ba, idan ina kukan na rasa saurayi sai ka rufeni da fadan me zan yi da wani saurayi? TAUFEEK ka cika rigima ka sani kuwa?" "Kin fini iya rigima, kiri kiri kike neman ajiye hijab ki fitar min da nutsuwata fili!, Kin fini iya rigima tunda kike min kukan saurayinki, hey wife kin fini iya rigima tunda kika iya riken wuya kuma ki nemi auren wani!" Ya fada yana dago fuskarta a hankali ya hade bakinsu waje daya Sai da ta ga yana neman tsallake iyaka ta nusar da shi da kyar tana fitar da shashekar gajiya ta yi lufff saman kirjinsa a zuciyarta tana tunanin ya san yana sonta ya auri Yumnah? Sai dai ba zata taba iya yi masa wannan tambayar ba dan ta san abin ba wani dadin ji Cikin shaukin nan da kauna Khausar ta karashe kwanakinta na amarci, wa'inda TAUFEEK ya tsare gaba ya tsare baya ya hannata fita har sai da ta cike su sannan ya yarda ta je ta wuni bangaren su Mama da Hajia a ranar da Yumnah ta dauki girki Ba ita ta dawo falon ba sai da magariba ta shigo Bata tsaya wata wata ba ta yi dakinta ta shiga wanka ta fito ya gabatar da sallar isha sannan ta mike ta yi nafila ta wuce wajen turarukanta ta mutsitsika wa'inda suka kwonta mata ta koma saman gadonta ta kwonta idannuwanta saman wayarta ama hankalinta da gangar jikinta sun yi wajen da ruhinta ke bege, wato duniyar mijinta Kamar wasa barci ya nemi gagarar idannuwanta, dan haka ta mike ta dauko carbinta ta shiga salatin Annabi tana jin wani irin gurno mai fili a zuciyarta na rashin shi a gefenta! Idannuwanta ta dago a hankali tana kallonsa a lokacin da ya bude dakin ya shigo A hankali ta kauda dubanta gannin ya karaso ya duko daf da fuskarta Kasa kasa ya ce" Baki jira na zo ba kika shigo? Baki yi missing dina ba?" Khausar ta sauke ajiyar zuciya tana shaƙar kanshin abin wanke bakin da ya yi anfani da shi ta iskar bakinsa A hankali take kallon bakin nasa, tana jin irin abinda ke tsikararta Idannuwan nata ta nemi yin kasa da su dan ta daina kallon abinda zuciyarta ke maraita mata, sai ta ji samun abin cikin salama a lokacin da ya bata ba tare da ya ja ranta ba Ajiyar zuciya ta sauke a hankali ta cafke leben ta shiga tsotsa harda sakin wata irin ajiyar zuciya A hankali ta saka hannunta tana tare kokarinsa na son hayowa saman gadonta, muryarta a raunane ainun ta ce" Good night" Irin yadda kirjinsa ke bugawa sai ya baka tausayi, fa kyar ya saki rigarta ya mike yana kallonta kasa kasa ya ce" Ki shirya gobe mu je aiki in sha Allah" Yana gama fada ya fice ita kuma wannan bayani ya sakata hantsilowa daga gadon cike da farin ciki ta karasa wajen tufafinta tana ta aukin sakin murmushi ta shiga fitar da abinda zata saka dan komawa bakin aikinta cike da jin nutsuwa a jikinta Koda suka gama dukkan abinda zasu yi da Yumnah da ya kwatanta hakinsa shi da kansa ya yi hakuri domin cikin nata yana wahalar da ita, ga kuma kwanakin nan da ta daga hankalinta danma ya kula kwana biyun nan sosai ta rage damuwar nan a dole ya yi kwonce gefenta idannuwansa a bushe cike da bukatar iyalinsa a zuciyarsa! .............. 💔💔💔💔❤‍🩹❤‍🩹💔💔💔💔 *DA CIWO A ZUCIYATA* 💔💔💔💔❤‍🩹❤‍🩹💔💔💔💔 _MALLAKIN_ *SAJIDA NIJAR* *FREE BOOK NE* 6️⃣1️⃣ *GARABASA, GARABASA, PROMOTION, PROMOTION DIN LITATAFAN MARUBUCIYAR A KAN FARASHI MAI SAUKI 1K, YAN NIJAR KUWA 1000 FRANCS CEFA* 1: Duk karyar kada 2: Yar mahaukaciya 3: Neman na kaina 4: Bani da zabi 5: Bak'a ce 6: Kutkale 7: Makauniya ce 8: Mage 9: Duk nisan jifa 10: Idan ka raina inda kake 11: Dutse 12: Alkalamin kadarata 13: Bani da zabi 14: Dakika Biyar 15:Wata kokowar 16: Aure yakin mata 17: Ni zan ladabi 18: Daga tafia daukar soja *Dukansu a kan farashi mai sauki, zaka saka dubu guda ne domin promotion ne nake yi, ka tuntubeni kan layina kamar haka +227 93 81 16 18, Sajida Nijar* Now *Da CIWO A ZUCIYATA* *Tallah, tallah, tallah* *SECRET DE LA FEMME DU MANGA* _Gidan Kamshi, Sirrin Manyan Mata, nesa tazo kusa,Amarya ,Uwar gida,Ango da mai gida Har ma da yan mata da samari shin kuna sane da cewa HAJIYA FUSAM ta shirya tsaf domin gwangwaje ku da turarakunta masu dankaran kamshi? Tare Kayan gyaram jiki na musamman ,wanda daga nesa kamshin ki kadai ya wadatar ya isar da sakon zuwanki waje,gidan ki kuwa sai ya zam abun kwatance wajen kamshi, kar na cika ku da surutu bara in fara zayyano su_ Farar Humura Bakar Humura Humura special, humura de bain Humura epicé Lait de nuit Parfums désodorisant Parfums rideau et dras Lait de nuit Alkam Kulakcam *Waɗannan kadan ne daga bangaren turaran ruwa* Gagab, sandal flex, Durot, durus, sandal fleur, tafarce, farce, sandal bangui, sandal, hypotonic sandal, al'ut, coktail creation VIP, Gajiji, Mankaji, turaran wutar labule da cafet, Aba malan, boulettes *Munada bangaren gyaran jiki kamar haka:* mai mai saka santsin jiki, mai mai kanshi, Kayan gyaran jiki mai saka fata ta yi santsi da laushi, kayan gyaran jiki mai saka fata ta yi fari, Sabulu mai saka fata ta yi haske, sabulu mai saka fata ta yi santsi, sabulu mai goge yanayin fata, mai wanda baya saka fari mai gyara fata Sayen na gari mai da kudi gida,sai an gwada akan san na kwarai💃💃 Hajiya Fusam na zaune a kasar Niger domin yin magana da ita kai tsaye tuntuɓi wannan number 97 82 44 94 *SECRET DE LA FEMME DU MANGA* Gidan Kamshi, Sirrin Manyan Mata💃💃💃💃💃 Tallah 3 Hajiata, ke kin san rayuwar aure sai da anini, in babu jagab a babar eriya oga ya kama tofa yawu da neman yadda zai yi bawan Allah, idan kuma babar haja a bude ham ai ba labari oga sai dai ya shiga ya fito kamar ya shiga kofar ruwa😔, zo ki ji, a farashi mai rahusa zaki gwangwaje ki rike bakin Elhaji gudun tada yara, ama idan lamari ya yi lamari tsaf zaku karya gado☹️🫣 🔥💥🔥💥🔥💥🔥💥🔥💥🔥💥🔥💥 *HOHOHO WANI KAYA SAI AMALE, DON JAKI BAZAI 'DAUKA BA, INA MATA MASU BUK'ATAR 'DAGA DARAJARSU A WAJAN MAZAJENSU INA MATAN DAKE SHAN WULAK'ANCIN MIJI KO NA KISHIYA ,INA MATAN DAKESON ZAMOWA MOWA AGIDAJEN AURENSU TO ALBISHINRU MAMAN ZARAH YAR MUTAN SOKOTO TA SHIRYA TSAF DOMIN GABATAR MAKU DA ZAFAFAN KAYAN MATA MASU KYAU DA INGANCI WANDA BASUDA ALGUS ACIKI , AKWAI MAGANI DANAYI BINCIKE AKANSU DAN FARIN CIKIN MA'AURATA NAMU BA IRIN NASU BANE KAYAN MU NA DABAN NE NA ASALIN SAKKWATAWAN SHEHU MASU ABUN MAMAKI* 07034251528 kayanmu masu inganci ne masu ladaftar da kowane irin namiji Kad'an daga cikin abubuwan da muke dasu Ingantaccen maganin nono , Wanda zai gyara maki nononki donmin dawo da martaban nononki acikin kankanin lokaci komai lalacewarshi kuwa sauran bayani sai mun had'u pc +234 703 425 1528 Maganin hips (hips up) Wanda zai ciko maki da hips dinki su cika suyi bul bul ga laushi dasu k'ara suyi dass abun sha'awar kowane namiji Maganin infection Sha yanzu magani yanzu Yana fatattakar sanyi cikin kankanin lokaci magani ne na maza da Mata insha Allah kowane irin sanyi gareki kikayi amfani dasu anwuce wajan Ingantacce Kuma sahihin maganin k'iba Wanda Zaki ciko acik kankanin lokaci zakiyi kibar ki Yar dai dai misali ki huta Zama da Rama Baki rasa ci ba Baki rasa sha ba amma kullum Ana kallon cewa kinada matsala agidan aurenki saboda wannan ramar , Rama batayi ba Sam Yar uwa Sabulun wanka Kalolin sabulun tsarki Turaren tsugunno Turaren al'ajab Hatsabibin turare Da sauransu 07034251528 Kalolin gumba Gumbar Dabino Gumbar gero Gumbar madara Gumbar matsi Gumbar ukku bala'i Gumbar tada zaune tsaye Gumbar sabon budurci Gumbar sa buzu kuwa Gumbar aya da kwakwa Gumbar ridi Gumbar mazari Sarauniyar gumba 3in1 Da sauran kalolin da bansamu fadi ba, Kalolin gari Garin mallaka Garin hutar da malaminki dakan jaraba Dakan Amare Dakan Ni'ima Dakan kishiya in bakiyi bani waje Garin sa buzu kuwa Garin buje.sharkaf Garin Dan la'asar Yayan hadiya mai suna dan la'asar Original Dan goshi Original Dan goshi (sabon salo) Original man damo Original man ayu Kitsen damo Sirrin tafin kafa Sirrin farinjini na uwargida da amarya harma da yan mata Kwallin idonka idona Muna hada set na sirrin mallaka hajiya ba boka ba Mallam sai tarin sirrika kema kizama kowa agidan surenki Akwai hadin sabon budurci ga yarinyar data rasa budurcinta ta hanyar fyade ko yaudarar d'a namiji da izinin Allah akayi maki wannan hadin to an wuce wajan sauaran bayani sai mun had'u pc Kalolin tsumi Tsumin mallaka Tsumin jaraba Tsumin madarar ni'ima Tsumin tabaje Tsumin Amare Tsumin sabon budurci Tsumin nono rakumi Matan gaske Ruwan jaraba, Da sauran kalolin da ban fada ba Kalolin matsi da basuda illa ajikin mace sai dai ma sukara maki lafiyar Matsin Dan mannau Matsin mallaka Dan la'asar Sabon budurci Mak'alemata Mashahurin matsi Ukku bala'i Matsin uban budurwa Akwai gumba ta matsi wadda Shanta akeyi ga matan da basa son yin matsi Muna hada set ga wadda Allah ya jaranfa da matsalar fyade har yarasa budurcinta , muna hada mata kaya ingantattun don dawo da martabar ta, Hohohohoho in ana dara fidda uwa ake *Kyallen al'ajabi* babban sirrin mallaka mai abun al'ajabi mallaki naki don samun damar shiga cikin jerin mata masu fada aji a gidan mazajensu , KARKU manta da sunan maman zarah sokoto sayen nagari maida kudi gida 07034251528 ina maraba daku sayen daya ko sari ina Sokoto sannan ina aikawa kowane gari cikin aminci da yardar Allah Ga Wanda suke bukatar ganin kalolin kayana to suyi sarving number na suyimun magana nayi sarving number ku zaku dinga ganin kalolin kayana a status ngd sosai 07034251528 Maman zarah mabera SOKOTO Washe gari karfe bakwai da rabi ya sauko, a lokacin tuni Khausar ta gama girkin abin kari ta yi shiri irin na wace zata fita da sassafe A wajen dinern take tsaye tana sake gyara wajen a nutse ta juyo tana sauke dubanta saman fuskarsa A hankali ta sake ambaton sunnan Allah a cen kasan zuciyarta , domin tunda ta sauko aikin nan karfe biyar take sake saken ko yana ina? Bata ji fitarsa masalaci ba, ama ta ji dawowarsa, haka kuma bata san wani dakin ya je ba nasa ko na matarsa , abinka da shedan sai ta ringa yan dake sake masu zafi a zuciyarta, sai dai cikin ikon Allah bata bari abin ya mata ila ba ta ringa ambaton Allah da kuma sakawa ranta cewar Yumnah iyalinsa ce bata da ikon saka wani abu a rai dan ta yi tunaninsa da ita , hakan wata hanya ce ta sakawa rai damuwa, gwara zikiri da wannan tunani, dan haka sai ta bige da zikirin Murmushi ta sakar masa kamar yadda ya sakar mata sannan ya bude mata hannayensa A nutse ta karasa ta shige jikinsa a hankali ta lumshe idannuwanta tana shaƙar kanshin turaran da yake yi kasa kasa ta ce" Barka da safiya Magidanci" Murmushi ya yi a hankali ya ja hancinta sannan ya dan juya wajen dinern kasa kasan shima ya ce" Iyalina....., Fatan kin tashi cikin koshin lafiya?" Murmushi ta yi a hankali ta amsa shi sannan ta nuna masa abin karin tana fadin" Ga abincin , na kirawo Yumnah ne mu karya?" Sakinta ya yi ya karasa bakin kujera ya ja ya zauna yana kallonta ya ce" Dan bani abu a frij mana?" Juyawa ta yi ta karasa wajen frij din ta bude ta dan duka sannan ta juyo tana kallonsa ta ga ya mata wani kuriii ta ce" Me zan dauko?" Idannuwansa ya dauke a hankali ya girgiza kai da hannunsa ya yafitota Dan jim ta yi kafin ta rufe ta dawo inda yake tana sauraronsa Hannayenta biyu ya riko yana kallonta a tausashe ya ce" Anya kuwa zan iya?" Khausar ta zuba masa ido, a hankali ta ce" Mene ba zaka iya ba?" TAUFEEK ya sauke ajiyar zuciya a nutse ya dago yana kallon fuskarta daga irin riko hannayen nata da ya yi ya ce" Da ace ba zan tauye hakinki ba, da mun je na saka hannu a gaban mai kwanoni cewar du karshen wata zaki dauki albashinki ki zauna a gida, a gidanma a bangarena....., Khausar kin yi shiga kamilaliya ama kuma idan kika juya kina min wasa da ajiya, dole sai sun motsa ne?" Ido ta rintse cikin jin matsananciyar kunya A hankali take son kwacewa dan ta boye fuskarta ama ya ki bata dama A tausashe ya dora da fadin" yaya zamu yi? Ko mu yi hakan?" Da sauri ta bude idannuwanta ta zuba masa su, eh ta sani albashinta ba komai bane a wajensa idanma du sati sati zai mata ba zai taba gajiyawa ba, sai dai yau da gobe akace, tunda ta riga ta zama iyalinsa zama ne za'a yi na sabo, komai kyanta komai son da yake ji nata a zuciyarsa yau da gobe na iya goge komai a ransa sai kauna da girmamawa idan ta yiwa kanta da kyau ta zauna lafiya da shi , ba ita daya yake da ita ba, kuma bata da tabacin daga ita zai rufe ne ko kuwa zai samu wace ta fita ne? Ko ba komai namiji ne shi wanda Allah ya halitta da bukatar hakan da kuma yan leke leke irin na ido da zuciya idan yau ta dauki wannan dama ta rike me gaba zata haifar? Gwara ya zamto an yi abin a bisa tsarin da ya dace , to fa za'a iya tsofewa ana yi...., ko ba wannan ba ai bata yi karatun likita ba dan ta zauna a gida ba tare da tana yin aikin ba, tana so, tana kwadayin ladan nan sosai A tausashe ta dan yi kasa da dubanta ta ce" Ka yi hakuri, in sha Allah dukkan abinda na ga zai daga maka hankali zan kiyaye, ama Please ka daina maganar nan mana *ABINMU?* " Ajiyar zuciya ya sauke kawai ya shiga cin abincin da ta zuba masa bayan ya tabatar mata Yumnah ɓaci take yi, dan bata cika kari da safe ba gaskiya shima har ta kusan koya masa haka Hajia ce ta ki hakan dan in bata bashi karin ba ita ke bashi tana fadace fadace Sai da suka gama ta haye saman ta sako hijab dinta ta dauko jakarta ta hannu baka sannan ta shafa dan sasaukan turare sai agogon dake hannunta da zobunna biyu na azurfa , takalmin kafarta kuwa plate ne baki irin jakar mai kyan gaske sai wayar da ta fara zame mata jiki saboda irin yadda yan uwanta ke saka mata riketa a rai ta hanyar tabota ta whatup da sakata a grups na karuwa na matan da suka san kansu A lokacin da ya nufi bangaren su Mama ita kuma ta yi na Hajia, a gagauce ta amshi abinda Hajiar ta jika wai ko maganin baki ko me ta sha ita dai sannan ta yiwu Hajiar salama ita kuma ta rakota har bangaren su Maman tana faman mata addu'a A nan suka hade da shi , a lokacin da ya gane ta zo yiwa mama salama ne zata je wajen aiki sai ya ji wani dadi a ransa, Bama da ya ga Maman ta riko hannunta ba wani kawar da kai irin na sirikan nan ta yi mata addu'a harda su gyara mata hijab dinta sai ya ji wani irin farin ciki ya idasa lulube shi Har sun shiga Mota Hajia ta bata nasa maganin bakin ta ce" Bashi ya sha, Ni ya rainan wayo ba zai sha ba" Khausar ta yi murmushi ta amsa ta juyo gefensa a lokacin da ya sakarwa Hajia Harara ya ce" Kauce Ni in ja motata!" Hajia ta tabe baki ta ja baya tana sakarwa motar naushi kuma ta yarfe hannun ta ce" Aikin banza motar banza da wofi gareka wata mota irin ta munafukai na waje baya gannin na ciki sai dai na ciki ya ga na waje, da ire irinsu ake satar ya'yan mutane, a ciki kuma ake yiwa ya'yan mutane ciki!" Ido ya zarro ya juyo ya kalli Khausar Ita kuma bata shirya ba ta fashe da dariya har tana rike ciki ta dora hannayenta biyu saman kanta ta ce" Na shiga ukuna me yasa kake son saka Hajia fada ne a rayuwa?" Shima dariyar ya yi yana ficewa da motar a gidan sannan ya harbata bakin titi ya ce" Hajia bata jin magana " Ita kam rabonta da daria irin haka har ta manta, a haka suka karasa wajen aikin A lokacin da suka fito daga motar ya zamto ne lokacin isowar manyan, kuma idan an iso din sukan dan tsaya su gaisa ne kafin kowane ya nufi bangaren da yake aikin wato manyan doctocin asibitin Lokaci daya yannayinsa , wanda ta ganshi a lokacin da ta zo asibitin ya wanzu a tare da shi da fuskarsa baki daya Bayan ta fito a motar sai ta samu kanta da satar kallonsa, dan kuwa gaba dayansa sai ya sake kawatuwa a idannuwanta A nutse ta zagayo da nufin tafiya ta shige bayan ta gaisar da likitocin domin a irin lokacin du sun ga shi din ne a motar dan haka sunna haramar fara gaisar da shi a matsayinsa na baban su kuma abokin aikin su A hankali ya kamo hannunta, sannan ya janye jakar hannun nata ya rike a tausashe ya ce" rigarki a office dina fa, mu je ki saka" Jakar ta bi da kallo sannan ta kalli abokan aikinsa wa'inda suke manyan ta ita kuma, Da sauri ta sada kanta ta koma gefe kadan da girmamawa ta shiga gaishe su, a cikinsu daya ne kawai ya san mata take a wajensa, shine wanda ya kula da Hajia ranar da aka kawota dan haka da kula sosai ya amsa gaisuwar yana fadin" Barka da isowa madame" Sauran kuwa du sai abin ya sake basu mamaki, bale matan cikinsu Docter Umaima ta ce" Docter kawo jakar na rike" TAUFEEK dake gaisawa da mazan a nutse ya dan girgiza kai ya ce" Ta madame ce Zan rike docter, thank you" Daga nan ya karasa da ido ya mata alamun ta yi gaba dan haka ta juya ga yi gaban tana lumshe idannuwanta dan hanna kirjinta dokawar nan ta fara shigewa lft din shima ya shiga ya danna ya rufe su sannan ya yi sama da su "Professeur aure ya karra ne?" Docter ta tambaya cike da mamaki Docter ya ce" Eh matarsa ce, haka dai ya fada min ranar da aka kawo Hajia" "Wauh ashe mugun dan soyaya ne? , Ka ga a irin yadda baya sakarwa matan wajen nan fuska ban yi zaton zai iya zuba soyaya harda rikewa mace jaka ba" docter Aliyu ya fada yana murmushi, har ga Allah ya manta cewa Docter Mufeeda na fama da kai kawo irin na soyaya a zuciyarta na ogan nasu, sai da ya ji ta ja tsaki ta yi gaba da jakarta ta nufi bangaren da take aiki wato itace shugabar su KHausar din ta barsu a nan ne ya zarro ido a ransa ya ce" Toh fa" Sai da ya Bala mata boturan rigar kaf sannan ya barta ta tafi wajen aikinta bayan ya yi mata kashedin karfe goma sha biyu maza ta hayo ta ci abinci ko me take yi zai tanadar mata abincinta ya bata ky din office din koda baya nan ta bude ta ci ta koma A lokacin da ta sauko ta je stf dinsu tuni an shiga aiki, sai dai tana zuwa yau din ta hadu da aiyuka harda na mamaki, domin tarin yan pansamar da aka yiwa aiki ne ke jiranta ba sakin fuska ba komai docter Mufeeda ta umarceta kan ta hau aiki bayan ta mata fadan dora lokacin da ta yi gaban kowa ta dizgata da fadin ba fa zata dauki irin wannan abin ba, ta kula aiki ya kawota ba biye biye ba Sosai Khausar ta tsorata da yannayin docter, dan bata taɓa ganninta tana masifa haka ba, hasalima bata san menene laifinta ba ama gudun karawa kanta wani laifin sai ta shige dan dakin ta shiga aikin ba ji ba gani a tsaye ne ba a zaune ba A kala ta kai awa uku tana aikin nan dan asibitin ba karamar asibiti bace, yan fashin kuwa ba iya na haihuwa bane Tana gamawa ko ruwa bata bari ta sha ba ga abokan aikinta ga komai sunna zaune sunna dan hutawa da yar fira docter tace" ki je dakunna ki duba duk wanda karin ruwansa ya kare ki cire in an karra masa wani ki kara in ba za'a kara ba ki masa bayani" Da dan mamaki Khausar ta ce" Docter duka dakunnan ?" Docter Mufeeda ta ce" Eh, akoy damuwa ne?" A hankali ta girgiza kanta ta je tana harhada kayan aikin tana jin juwa na dibanta sosai, sai dai ita ta san ba wai dan ta yi wannan dan aikin bane domin wanda ya samu horon hospital urgence karya ne aikin tsaye ya saka shi juwa Tana gama hadawar sister Humaira ta mike tana turo abin turawan nan ta ce" Dora mu je sister" "Ita kadai zata yi!" Docter Mufeeda ta fada tana gimtse fuska ta ci gaba da aikinta Gaba dayansu hakan ya matukar basu mamaki, kowa sai ya saka a ransa ko laifi Khausar din ta yi? Ciki harda mazan domin daya sai da yace" Docter ko sister Khausar ta yi laifi ne? A gafarceta abu da bako?" Ama sai docter ta masa banza ita kuwa Khausar a haka ta fice ta shiga aikin nan cike da kula da mutunta marar lafiya Wannan zagaye sosai ya saka ta gaji, ko dan ta kwana biyu bata yi bane? Ko menene? Koma dai menene gaskiya ji take yi kamar ta kifa ga wata juwa dake janta sosai, a haka ta karasa office din nasu ta ajiye chariot din sannan ta daura alwallah ta shiga sallah dan a lokacin tuni an yi azahar Tana gamawa ta fito da nufin zuwa ta ba docter hakuri ko wani laifi ta yi? Ba dan ta ringa sakata aiki ita kadai bane, ko daya, yannayin fuskar na docter ne ya sakata a damuwa, dan bata saba ganninta tana masu haka ba sam, eh lalle mace ce mai kamewa ama ba har haka ba, karrara fuskarta na nuna kamar tana jin haushinta ne Tana fitowa wani ikon Allah ko damar ta je cin abincin ita yau Docter ba zata bata ba da wani daure fuskar ta ce" Ki je daki mai numbar ashirin da daya ki goge amai patient din ya yi" Da dan mamaki ta zuba mata ido, gugar amai kuma? Gugar amai fa?, Yaushe asibitin ta fara hade hade ne kuma bayan akoy wa'inda wannan din ne aikinsu ita likita me ya hadata da zuwa gugar amai, Da kula sosai da kuma girmamawa Khausar ta ce" Docter gugar amai? Babu masu yi ne?" Docter ta dago da mamaki tana dubanta ta ce" Sai babu masu yi zaki yi? Ko ban isa sakaki ki yin bane?" Da sauri Khausar ta dan girgiza kai tana sada kanta ta ce" Ki yi hakuri ba haka nake nufi ba, bari in je in yi, dan Allah idan na yi wani laifin ne ki gafarceni docter" Docter zata yi magana aka sake dan kwankwasawa dan haka ta dago a dan fusace ta ce" Com in, wai wanene dan Allah!" A nutse ya murza kofar ya shigo yana sauke dubansa a kan docter Mufeeda wace ta zuba masa idon itama zuciyarta na dokawa da abubuwa masu yawa a cikinta Da kula ya ce" Barka da warhaka docter" Da kyar ta iya yakar bakinta har ta iya fitar da furucin bakin nata sada dubanta a tausashe tana kokarin boye damuwarta da kuma girmamawa a gare shi ta mike tana fadin" Professeur Barka da rana, ka yi hakuri dan Allah ina cikin aiki ne sosai shi yasa na amsa a haka" Bai ce mata komai ba sai Khausar da ya kalla, a nutse ya sake kallon Docter Mufeeda sannan ya kuma kallon KHausar Ledar dake hannunsa ta take a way ya mikawa Khausar din a tausashe ya ce"Ba nace karfe 12 ta maki a office dina ba Wifey????" Da sauri Docter Mufeeda ta dago ta zuba masa ido, Khausar kuwa da ta amshi abincin ta rike a hannunta ta kasa koda kallonsa ne dan idannuwanta sun ciko da kwallah ta dan sauke ajiyar zuciya a hankali ta ce" Aiki ne nake yi TAUFEEK, yanzu zan zo" Wani sake zarro idon Docter Mufeeda ta yi jin gatsau wannan ta kirayi Professeur da sunnansa? A nutse ta kai ledar ciki ta fito ta karasa wajen abin sharar nan ta dauki bokici guda da kayan aiki ta juya da nufin tafiyarta A dan daburce Docter Mufeeda ta ce" AM, sister Khausar dawo ki ci abincin mana" Khausar ta ja ta tsaya , ta juyo tana kallonta sai kuma ta kai kayan ta ajiye ta koma ta dauko ledar ta fito Da kyar ya iya budar bakinsa da ya wani irin dafkewa da bacin rai ya ce" Ki je office dina" Khausar ta gyada kai ta wuce, ita ba abinda ya fi damunta irin juwar nan ta nufi sama Da mamaki ya zubawa docter Mufeeda ido yana kallonta ya ce " 💔💔💔💔❤‍🩹❤‍🩹💔💔💔💔 *DA CIWO A ZUCIYATA* 💔💔💔💔❤‍🩹❤‍🩹💔💔💔💔 _MALLAKIN_ *SAJIDA NIJAR* *FREE BOOK NE* 6️⃣2️⃣ *GARABASA, GARABASA, PROMOTION, PROMOTION DIN LITATAFAN MARUBUCIYAR A KAN FARASHI MAI SAUKI 1K, YAN NIJAR KUWA 1000 FRANCS CEFA* 1: Duk karyar kada 2: Yar mahaukaciya 3: Neman na kaina 4: Bani da zabi 5: Bak'a ce 6: Kutkale 7: Makauniya ce 8: Mage 9: Duk nisan jifa 10: Idan ka raina inda kake 11: Dutse 12: Alkalamin kadarata 13: Bani da zabi 14: Dakika Biyar 15:Wata kokowar 16: Aure yakin mata 17: Ni zan ladabi 18: Daga tafia daukar soja *Dukansu a kan farashi mai sauki, zaka saka dubu guda ne domin promotion ne nake yi, ka tuntubeni kan layina kamar haka +227 93 81 16 18, Sajida Nijar* Now *Da CIWO A ZUCIYATA* *Tallah, tallah, tallah* *SECRET DE LA FEMME DU MANGA* _Gidan Kamshi, Sirrin Manyan Mata, nesa tazo kusa,Amarya ,Uwar gida,Ango da mai gida Har ma da yan mata da samari shin kuna sane da cewa HAJIYA FUSAM ta shirya tsaf domin gwangwaje ku da turarakunta masu dankaran kamshi? Tare Kayan gyaram jiki na musamman ,wanda daga nesa kamshin ki kadai ya wadatar ya isar da sakon zuwanki waje,gidan ki kuwa sai ya zam abun kwatance wajen kamshi, kar na cika ku da surutu bara in fara zayyano su_ Farar Humura Bakar Humura Humura special, humura de bain Humura epicé Lait de nuit Parfums désodorisant Parfums rideau et dras Lait de nuit Alkam Kulakcam *Waɗannan kadan ne daga bangaren turaran ruwa* Gagab, sandal flex, Durot, durus, sandal fleur, tafarce, farce, sandal bangui, sandal, hypotonic sandal, al'ut, coktail creation VIP, Gajiji, Mankaji, turaran wutar labule da cafet, Aba malan, boulettes *Munada bangaren gyaran jiki kamar haka:* mai mai saka santsin jiki, mai mai kanshi, Kayan gyaran jiki mai saka fata ta yi santsi da laushi, kayan gyaran jiki mai saka fata ta yi fari, Sabulu mai saka fata ta yi haske, sabulu mai saka fata ta yi santsi, sabulu mai goge yanayin fata, mai wanda baya saka fari mai gyara fata Sayen na gari mai da kudi gida,sai an gwada akan san na kwarai💃💃 Hajiya Fusam na zaune a kasar Niger domin yin magana da ita kai tsaye tuntuɓi wannan number 97 82 44 94 *SECRET DE LA FEMME DU MANGA* Gidan Kamshi, Sirrin Manyan Mata💃💃💃💃💃 Tallah 3 Hajiata, ke kin san rayuwar aure sai da anini, in babu jagab a babar eriya oga ya kama tofa yawu da neman yadda zai yi bawan Allah, idan kuma babar haja a bude ham ai ba labari oga sai dai ya shiga ya fito kamar ya shiga kofar ruwa😔, zo ki ji, a farashi mai rahusa zaki gwangwaje ki rike bakin Elhaji gudun tada yara, ama idan lamari ya yi lamari tsaf zaku karya gado☹️🫣 🔥💥🔥💥🔥💥🔥💥🔥💥🔥💥🔥💥 *HOHOHO WANI KAYA SAI AMALE, DON JAKI BAZAI 'DAUKA BA, INA MATA MASU BUK'ATAR 'DAGA DARAJARSU A WAJAN MAZAJENSU INA MATAN DAKE SHAN WULAK'ANCIN MIJI KO NA KISHIYA ,INA MATAN DAKESON ZAMOWA MOWA AGIDAJEN AURENSU TO ALBISHINRU MAMAN ZARAH YAR MUTAN SOKOTO TA SHIRYA TSAF DOMIN GABATAR MAKU DA ZAFAFAN KAYAN MATA MASU KYAU DA INGANCI WANDA BASUDA ALGUS ACIKI , AKWAI MAGANI DANAYI BINCIKE AKANSU DAN FARIN CIKIN MA'AURATA NAMU BA IRIN NASU BANE KAYAN MU NA DABAN NE NA ASALIN SAKKWATAWAN SHEHU MASU ABUN MAMAKI* 07034251528 kayanmu masu inganci ne masu ladaftar da kowane irin namiji Kad'an daga cikin abubuwan da muke dasu Ingantaccen maganin nono , Wanda zai gyara maki nononki donmin dawo da martaban nononki acikin kankanin lokaci komai lalacewarshi kuwa sauran bayani sai mun had'u pc +234 703 425 1528 Maganin hips (hips up) Wanda zai ciko maki da hips dinki su cika suyi bul bul ga laushi dasu k'ara suyi dass abun sha'awar kowane namiji Maganin infection Sha yanzu magani yanzu Yana fatattakar sanyi cikin kankanin lokaci magani ne na maza da Mata insha Allah kowane irin sanyi gareki kikayi amfani dasu anwuce wajan Ingantacce Kuma sahihin maganin k'iba Wanda Zaki ciko acik kankanin lokaci zakiyi kibar ki Yar dai dai misali ki huta Zama da Rama Baki rasa ci ba Baki rasa sha ba amma kullum Ana kallon cewa kinada matsala agidan aurenki saboda wannan ramar , Rama batayi ba Sam Yar uwa Sabulun wanka Kalolin sabulun tsarki Turaren tsugunno Turaren al'ajab Hatsabibin turare Da sauransu 07034251528 Kalolin gumba Gumbar Dabino Gumbar gero Gumbar madara Gumbar matsi Gumbar ukku bala'i Gumbar tada zaune tsaye Gumbar sabon budurci Gumbar sa buzu kuwa Gumbar aya da kwakwa Gumbar ridi Gumbar mazari Sarauniyar gumba 3in1 Da sauran kalolin da bansamu fadi ba, Kalolin gari Garin mallaka Garin hutar da malaminki dakan jaraba Dakan Amare Dakan Ni'ima Dakan kishiya in bakiyi bani waje Garin sa buzu kuwa Garin buje.sharkaf Garin Dan la'asar Yayan hadiya mai suna dan la'asar Original Dan goshi Original Dan goshi (sabon salo) Original man damo Original man ayu Kitsen damo Sirrin tafin kafa Sirrin farinjini na uwargida da amarya harma da yan mata Kwallin idonka idona Muna hada set na sirrin mallaka hajiya ba boka ba Mallam sai tarin sirrika kema kizama kowa agidan surenki Akwai hadin sabon budurci ga yarinyar data rasa budurcinta ta hanyar fyade ko yaudarar d'a namiji da izinin Allah akayi maki wannan hadin to an wuce wajan sauaran bayani sai mun had'u pc Kalolin tsumi Tsumin mallaka Tsumin jaraba Tsumin madarar ni'ima Tsumin tabaje Tsumin Amare Tsumin sabon budurci Tsumin nono rakumi Matan gaske Ruwan jaraba, Da sauran kalolin da ban fada ba Kalolin matsi da basuda illa ajikin mace sai dai ma sukara maki lafiyar Matsin Dan mannau Matsin mallaka Dan la'asar Sabon budurci Mak'alemata Mashahurin matsi Ukku bala'i Matsin uban budurwa Akwai gumba ta matsi wadda Shanta akeyi ga matan da basa son yin matsi Muna hada set ga wadda Allah ya jaranfa da matsalar fyade har yarasa budurcinta , muna hada mata kaya ingantattun don dawo da martabar ta, Hohohohoho in ana dara fidda uwa ake *Kyallen al'ajabi* babban sirrin mallaka mai abun al'ajabi mallaki naki don samun damar shiga cikin jerin mata masu fada aji a gidan mazajensu , KARKU manta da sunan maman zarah sokoto sayen nagari maida kudi gida 07034251528 ina maraba daku sayen daya ko sari ina Sokoto sannan ina aikawa kowane gari cikin aminci da yardar Allah Ga Wanda suke bukatar ganin kalolin kayana to suyi sarving number na suyimun magana nayi sarving number ku zaku dinga ganin kalolin kayana a status ngd sosai 07034251528 Maman zarah mabera SOKOTO A nutse ya zauna yana duban docter Mufeeda wace ta daburce ya mata nuni da kujerarta ya harda yatsunsa ya bata dama har ta zauna tana ta kokarin gannin ta hanna kanta rikicewa ama a bayane rikicewarta take, dan asibitin nan sunna da doka masu ƙarfin gaske da ake dukkan kokari dan kiyayewa "Akoy matsala ne da ya hanna masu aikin wanke datin patient yin aikinsu?" Ya fada ba da hargowa ko wani tashin hankali ba Docter Mufeeda sai da ta ja numfashi na tashin hankali a hankali ta girgiza kai ta ce" A'a babu sir" "Me yasa zaki saka Khausar wankewa? Me yasa a irin lokacin nan da kowa keda damar zuwa ya ci abinci idan har ba urgence GAREKU ba ita take nan tana aiki?" "Docter, aikinta ne bata gama ba shine yasa bata je din ba, kuma da ta gama sai nace ta wanke cen din dan an tabo mu ya yi aman gashi sun je cin abinci" ta fada tana dawurwuri da neman mafita Tsareta da ya yi da duban nan nasa ba tare da ya sake ce mata komai ba ya sakata shiga halin rikicewa Kanta ta dafe da hannayenta biyu ta ce" Dan Allah docter ka yi hakuri, ba zan sake ba in sha Allah kowa zai yi aikinsa yadda ya dace ka yi hakuri" "Idan kina da wata case da ma'aikatan da suke karkashin ki a matsayinki na baba, ki bi yadda ya dace dan a ringa mutuntaki , idan ta maki wani laifi ne ki shigar da kara , ko me tsakanina da ita zata dauki hukuncin da asibiti ta ɗorawa doka, ba zamu bari ma'aikata su raina ku ba, but ba zaku wulakanta su ba, kuma ki sani kamar yadda kike da damar kai karar ta maki tana da damar kawo karar kin mata, idan har tana da gaskiya Docter Mufeeda Muhammad doka zata hau kanki ne kuma ko ina kika je sai ta hau kanki dan kin san ban kafa asibitina ba sai da na tsaya da kaffafuwana, i'm i clear?" Wani irin yawu ta hadiya mai santsi da sauri ta gyada kanta tana ci gaba da bashi hakuri shi kuma ya mike ya yi tafiyarsa zuciyarsa na kuna da tunanin dolema Khausar ta saka kara dan ya samu damar wanke wannan matar, domin a haka ba zai hauta kai tsaye ba, shine zai taka dokarsa da kansa, ama inda yake godewa Allah ba wai manyan docter kadai keda ikon kai karar ba, harta wa'inda ke karkashin su sunna da damar nan! Yana nufar office dinsa ne yana lalubar numbar wanda ake ajiye kara wajenta Tana dagawa ya ce" Ki zo office dina" Bai tsaya ya ji amsarta ba ya katse, ita da kanta sai da ta ji hankalinta na neman tashi dan haka ta mike ta dauki dukan abin bukata ta nufi office din nasa cikin gagawa Yana shiga ya samu Khausar zaune saman kujera ta jinginar da bayanta, ga abincin da ya kawo mata a ledarsa bata bude ba, sai ruwa dake daf da kafarta da kuma madarar ruwa marar siga dake hannunta bata bude ba idannuwanta lumshe A nutse ya karasa bayan ya cire rigar dake saman farar rigarsa ya zauna daf da ita yana kamo hannunta da madarar sannan ya bude ledar yana fadin" Ya Salam, baki ci ba? Me yake damun ki? Me ta maki ne? Me ya haɗa ki da ita?" Khausar ta zuba masa ido, sai kuma ta saki murmushi a hankali ta yi niyar dora kanta gefen kafadarsa da niyar ce masa ba komai ba sai aka shiga neman izinin shigowa Dama ya bada yana kokarin saka Khausar yin abinda ta yi niya ita kuma ta janye tana gyara zamanta sosai har docter ta shigo tana mai yin salama da fadin " Barka da warhaka Professeur, gani " TAUFEEK ya sake riko hannun Khausar yana bata damar zama Sai da ta zauna ya ce"Na je bangaren docter Mufeeda ne sakamakon gannin lokacin da ya dace matata ta zo ta ci abinci ya wuce shiru, sai na tardata tana ta yi mata fada da cewar ta je ta wanke amai, yaushe aka cenzan tsarin asibiti nake son sani da kuma dalilinta na yiwa iyalina haka!" Daga Khausar din har docter a tare suka kalle shi,sai kuma docter Maimuna ta kalli Khausar tana fadin" Subahanallah, subahanallah, haka ya faru? A'a professeur babu wanda zai cenza dokokin asibitin nan ai sai kai kuma baka cenza mana ba gaskiya, gashi bata zo min da maganar daya daga cikin wa'inda ke aiki da ita ya mata wani laifi ba, koda laifin aka yi mata bata da hurumin daukan mataki da kanta ama bari yanzu yanzu na kirawota sai mu ji, in har wani abin ne ya faru a samu mafita ka yi hakuri, Madame dan Allah zan iya Sannin abinda ya hadaki da docter daga safe zuwa yanzu? Ko nace tunda kika fara aiki a nan?" Khausar da ta daburce ga kalli TAUFEEK ta kalleta ta ce" Docter dan Allah ki bar maganar, babu abinda ya hadani da Docter na san na yi wani laifin ne dan ba halinta bane gaskiya, kuma koda ban yi komai ba ai ta isa ta sakani aiki tunda gaba take da Ni, Ni dai a bar maganar nan dan Allah, TAUFEEK please bana so a bar maganar nan " Sosai docter Maimuna ta yi mamakin furucin Khausar, kai , to kuwa a ranta ta idasa yarda ba wancen madame din ta professeur bace, domin wancen din ba aikin likita take ba, kuma dai a yadda doctoci ke dan fadi sama sama haka sun nuna ita din rigimamiya ce sosai, ko ba wannan a wannan yannayin in wata ce ta samu damar TAUFEEK ba wai docter Mufeeda ba kowama sai ya fadawa yan garinsu a asibitin , sai gashi ita tana magana da girmamawa ta kuma nuna an isa da ITANE ya sa aka yi mata magana? A nutse ta dubi TAUFEEK, dan son ganewa in har yana amana da furucin matarsa, sai ta ga nasa fuskar a hade take bai wani bada damar a soke maganar ba kennan, dan haka ta mike tana fadin " A'a madame ki yi hakuri ai asibitinmu ba gidan tauye kowa bane gaskiya , dole a bi maki hakinki" Da sauri ta juya ta fice a office din, Khausar ta zuba masa ido a raunane ta ce" Me yasa zaka min haka? Ka san hakan na iya jaza min rashin zaman lafiya da ita bayan karkashin ta nake?, dan Allah ka ce masu ba komai karma a mata maganar, aikin kasheni zai yi ne? Ko menene zan iya yi mana, haba TAUFEEK sai ka sa a tsaneni cikin abokan aikina" Banza ya yi mata ya fitar da abincinta yana faman ta ci, domin ba zai iya ce mata komai ba sai tension dinsa ta sauka, sai dai ta yi hakuri dan babu wanda zai wulakanta masa ita ya kyale shi, ko waye kuwa sai dai inda ba zai iya ba ya fadawa Allah wato iyayensu, bayan su baya tunanin zai yarda wani ko wata ya wulakanta masa mata, in tana da laifi ok zai san yadda zai bima abin, ama fa a yadda ya san matarsa bata da wani laifi karya ne kuma a wukakantata a wajen da ta isa ! Yana faman ta cin ita kuma ta dage sai ya yi kiran docter Maimuna yace a bar maganar aka sake neman izinin shigowa Dan jim ya yi dan ya tabbata sun masa zuwan taron dangin nan kamar yadda suka saba in ransa ya bace a kan daya sukan zo ne baki dayansu a bashi hakurin abin, gashi shi rigimar yake so a yi gaskiya dan an fa tabo shi Da kyar ya bada damar su shigo Ai kuwa kamar da wasa doctors suke shigowa karshe docter Mufeeda ta shigo kanta a kasa idannuwanta har sun haye dan kuka domin ita ta gama YANKEWA cewar korarta zai yi, saima da ta ga docter Maimuna hankalinta ya idasa tashi, docter ta mata tassss ta mata fadan hakan dan bata da wani dalili sannan ta sakota gaba da manyan likitocin dake iya tankwasa shi a bashi hakuri, a nan ta sanar masu kaf cewar matarsa ce, Docter Mufeeda ta wulakanta A yadda yake zaune da cokali a hannunsa yana rike da hannunta daya bai cenza yannayi ba, bayan sun shigo dinma kallo daya ya masu ya sake duban KHausar ya ce" Ha mana bada na son gardama ba zaki ci abincin ba?" KHausar ta tsare shi da kallo tamkar zata saka ihun kuka A raunane cike da rikicewa ta ce" Ni zaka ma haka ko? Ni ko?" Sai ga hawaye sun bale mata ta sada kanta tana jan ajiyar zuciya Docter Maimuna ce ta saki murmushi gannin ya maido hankalinsa kansu ya harde yatsunsa yana kallonsu Docter Aliyu ya yi murmushin shima ya ce" A gafarcemu professor, in sha Allah laifin da muka aikata ba zamu kuma aikata makamancin sa ba, a yi hakuri Nan kowane idan ya budi baki hakurin ne yake badawa har aka zo kan Docter Mufeeda Tana fara magana itama sai hawayen ta sada kanta ta ce" I'm sorry sir, in sha Allah ba zan kuma ba, Madame ki yi hakuri ba zan kuma ba" KHausar ta girgiza kai da sauri , a hankali ta ce" Docter Walahi ba nice na hadaki da shi ba, Ni saima da nace ba komai , babu abinda kika min, dan Allah ku yi hakuri " "KHausar ya isa haka tashi ki shiga ciki" taufeek ya fada a tausashe yana kallonta Sai da ta sauke ajiyar zuciya sannan ta mike ta nufi cikin ta rufe Yana kallonta ne har ta rufe din sannan ya sauke ajiyar zuciya Sai kuma ya maida dubansa kansu ya basu damar zama sannan ya ce" Ya wuce, ba a kan Matata kadai nake iya yin haka ba, a kan kowa ne idan har na ga rashin adalci zan tsayawa ma'aikacina, kamar yadda kuka sani babu wanda ke raina ku, hakanan babu wanda zai wulakanta na kasa da shi dan Allah ya bashi dama, dan kina babba a wajenta nima baba nake a wajenki, ba wai maganar kina aiki karkashina ba a yau in sakamaki na yi du inda na hadu da ke ina iya cin zalinki, kin fahimta? Ina iya mayar maki da rayuwa cikin kunci in na so takuraki!" Su Dukansu dai hakuri suke ta bayarwa har ya gama fadansa ya salame su, sannan ya sake tarda KHausar wace ta cika ta cika sosai, yana shiga suka haura sama sai masifa take tana fadin yana son hadata da abokan aikinta , shi kuwa ya ringa bata baki cikin tausasawa har sai da ta shawo kanta ta sauko ta ci abincin sannan ya dauketa suka yi gida domin ya kula ba lafiya gareta ba sai tare kai take yi kuma ta ki yarda ya dubata tace juwa ce kawai dama tana yi in bata ci abinci a kan lokaci ba Koda suka je gidan wajen Mama ta je ta amshi jibda ta koma bangarenta ta shaka sosai, tana sakuwa ta sauko ta shiga kicin ta shiga girkinta hankali kwonce har ta gama ta koma dakinta ta kimtsa ta haye salayarta Kwonci tashi cikin Yumnah karra girma yake yi , inda ta karra ɗorawa kanta abubuwan da take gannin zasu fisheta, domin halaya raguwa dai suka yi ama ba barin su ta yi ba, dan kuwa koda ya nuna mata maganar kaura ita dake fatan a fidata daga gidan saboda takurar HAJIA a da, a yanzu ta ce ai ba inda zata je tana nan a dole aka shiga tada gini a dayan bangaren dake da fili dan KHausar ta koma, domin ya fada mata tunda ta ki komawa wancen gidan a nan din zata yi ta zama har yadda Allah ya yi Sanadiyar ginin nan da ake kyankyarawa matan mahaifinsa suka tada rigima ta mamaki, dan kuwa karara HAJIA Nawarah ta nuna uba fa ba na shi kadai bane, su da suke da mata ai su ne ya dace a ringa yiwa gurno mai kyau ba mutun baba kamar TAUFEEK ba wanda yake da shi kudin ama dan bakin ciki yana gindin na uba dan kar yan uwansa su samu Allah ya taima tsakaninsu matan da uban ne suka yi rigimar HAJIA bata sani ba shima TAUFEEK bai sani ba har aka gama ginnin aka kwaso kayan KHausar aka gyara mata bangaren ya zuba dukan abinda ya dace wanda zata rayu cikin walwala kamar yadda wancen bangaren ya malaka, kuma nan dinma dakunna ne har biyar kamar cen da kicin da komai Masha Allah Washe garin ta tare sai da Yumnah ta wuni gidansu, sai dai bata samu yadda take so ba domin ta tarda mahaifinta a gari yama na yi ya tarkatata ta koma gidanta da nasiha da tsaraba irin ta iyaye ga cikinta ya fito sosai dan a yanzu ya yi girman da ta kusa shiga watanta na haihuwa Bangaren KHausar tana rayuwa a cikin wannan familly ne tamkar tana rayuwa a familynta domin a watanni bakwai da ta yi a cikinsu zata iya cewa Alhamdulilah,dan kuwa tana ba duk wani wanda ya girmeta girmansa kuma tana kiyaye duk wata fitinar da za'a ce itace sila, tun daga kan HAJIA baba kuwa har auta ba zata ce ga wanda ya mata ido da ido ba, domin su auta idan mamansu ta fita fit suke su je bangarenta in tana nan su yi kallo su dan taba fira, dan irin yadda take jansu a jiki sun fi sakewa da ita fiye da Yumnah, domin Yumnah Akoy tsare gida, kuma tunda ƴaƴansu ya kara auren nan har iyayen nasu take baya baya da su , tana zuwa ama ba kamar da din nan ba da take zaunawa su yi ta sake sake tsakaninsu, domin yanzu har Mama tana zuwa ta gaisar sai dai babu wani abu tsakaninta da Maman bayan gaisuwar wace ta maidata kamar dole ne ba abinda ya dace ta yi bane dan isar abin a duniyarta, haka kuma tsakaninta da KHausar ido ne in sun hadu KHausar din na mata Salama takan amsa a takaice Shikenan dan kuwa bata tunanin zata iya yin wani dogon zumunci da matar mijinta! Tsakaninta da mijinta ne kawai tafia ke tafe ta fahimta da kokarinta na itama ta samu fuska yadda ya dace, Allah ya taimaketa shi din mai son kare hakokinta ne sai take samun kwonciyar hankali harda rigingimunta yakan Saurara ya kuma bata lokacinsa, sai abin ke kayatar da ita , ama a lokacin da ta so nuna ita zata je sabon ginin ne ya nuna mata bata da wayo sannan ya ja mata dogon kashedi a kan hakayar nan nata da fada mata nan fa da ta zaba ta yi kokari ya zama farin cikinta dan in dai ba ran Mai kwanoni ya bar gangar jikinsa ba kafin shi ya mutu ya bar duniya ya zama wajibi a rabawa ya'yansa gado ba, ba zai taba fidata daga nan ba, tundaga shi ta yi shiru da maganar take binsa Tsakanin TAUFEEK da KHausar fahimtar junna, soyayya, shawara daya , sunne suka fi komai tasiri a zaman har ya zamo koda ba a dakinta yake kwana ba tana makale a zuciyarsa ne, bale shakuwar da suka idasa sakawa a tsakaninsu bata da abin fadi sai godiya wa zabil izati, Taufeek duniyarta ne, shi din farin cikinta ne, kuma aikinta tana zuwa ba fashi Kwana biyu da kaurarta ta je gidansu weekend da kuma guzurinta na lalle dan a yi mata Tunda ta je maimakun a yi lallen sai ta yi kwonciyarta ta ce da Mama in an jima ta tasheta dan Allah juwa take ji sosai Sai dai bata iya tashin ba, sakamakon juwar maimakun ta saketa har sai da Aba ya dawo ya koma ya kawo wani magani da Mama ta saka ya kawo din ta shaka mata sannan ta ji ta saku har ta mike da mamaki ta nufi bayi dan yi alwallah domin lokacin sallah har ya wuce kuma TAUFEEK zuwansa biyu duka bata sani ba Tana shiga Bayi Aba dake sintiri ya shigo wajen Mama ya tsareta da ido Ya so ya yi shiru ama ya kasa a hankali ya ce" Mamansu, wannan magani rabona da na siyo shi tun kina da cikin Auta, ai da kika ce in siyo ni na zata auta ne ya girma tunda ba laulayi kike yi ba sai juwa da cin abinci" Yar dariya ta yi tana kallon Aba, wai auta ya girma, cabdijan ita yanzu ina ita ina raino, ciki baya bata wahala haihuwa ke wahalar da ita, domin idan tana da ciki babu mai sani sai in ta zo haihuwa , dan tana iya daukan wuni biyu tana fama bata samu kanta ba, yannayin jikinta ke boye cikinta ko shi babansu idan tace tana son maganin nan ne yake gane ta harbu kuma ba zata daina shaka shi ba sai ta haihu, bai sani ba ashe ta taɓa siyawa KHausar din tun bayan wata dayanta da tarewa da ta zo tana jin jirin nan zasu kai A'isha asibiti haihuwa ta siya mata shi ta bata take anfani da shi, to ya kare ne ta ci gaba da aiki da jibdar wajen HAJIA, inda HAJIA kuwa ke faman mata turare tana fadin sai ta yi da gaske juwa uwa wace ake son shiga gabanta? Shigowarta dakin maman da salama ya Hanna mama idasa fada masa na KHausar ne , tana shigowa ta ce" Mama, wannan abin Walahi yana da amfani, kin ga wanda kika banin nan ya kare ne dole na koma shaka jibda , Yayanmu wai wani Walahi wannan juwar ta fara daga masa hankali sai in je a min Alurai saboda juwa? Ni kuma na kiya nace na yi, ama zan bashi maganin nan ya kawo min da yawa sai in ringa anfani da shi ina ta addu'a har in warke " Aba ya sauke ajiyar zuciya ya fice a dakin, mama kuwa ta yi murmushi tana mamakin KHausar din, koda yake itama cikin KHausar din sai da ta kusa haihuwa cikin ya fara motsi ta fara tsorata tace ai cikinta ana motsa mata, nan ne fa aba ya kaita asibiti aka basu hoton ciki sunna yi aka ga yaro kwonce har ya dauki watanni takwas ba'a sani ba, to kuwa hakan ce ke shirin faruwa da KHausar dan cikin gaba daya a cinyoyinta ya sake badawa da kuma kirjinta , ya yi ham kamar ya yi magana , cikinta kuwa ba zaka gane tana da shi ba, ita kanta mai abin ba ganewa zata yi ba , yan wahalhalun da take sha a wajen miji kuwa ta dauka ne haka yake da wahala ta iya sabawa da yannayinsa, tana iya yinta dan gannin ta saba din tana kuma addu'a Ko da TAUFEEK ya dawo daukanta a zuwa na uku ta fito Aba ya bata leda shake da hanta mai zafi ya rakata har kusan motar yana ta Adu'ar a sauka lafiya ya dawo ya zauna zuciyarsa da tunanin yar yarsa kafin ya saka Mama a gaba kan sai ta fadawa Maman su TAUFEEK din dan a je asibiti, domin a irin yadda abin nan ya zama yanzu ci gaba ya samu ba'a wasa da harkar asibiti Da kunya da jin nauyi sosai Maman ta yi kiran numbar maman Taufeek Bayan sun gaisa cike da jin nauyi Mama ta ce" Mama dama, dama cewa na yi juwar nan ta KHausar ne, a je asibiti " Mama dake gyaran kayan Baba mai kwanoni ta dakata dan amsa wayar cike da damuwa ta ce" Mamansu juwar ta tashin mata yauma ko? Nima abin nan na damuna, du yadda na yi kuma sai ta nuna wai saboda juwa za'a je asibiti?, Hajiama cewa ta yi wai in bari ba aikin asibiti bane kin ga abubuwan da ta anso take Banka mata ba dare ba rana kuwa? Turare ne wanka ne, ama in sha Allah gobe goben nan za'a je asibiti nice nan zan rakata tunda idan ta kiya masa ban san yaya aka yi baya takurata ba bayan rashin lafiya ce ba abin wasa ba" Maman su Khausar ta yi dan murmushi tana matse ido dan kunya je dawainiya da ita a hankali ta ce" A'a Mamansu, ai Bama maganar wani ciwo bane in sha Allah, Inaga karuwa ne kawai dan awo ne nace bari in sanar domin ina kyautata zaton itama bata sani ba" Wani irin tsam mama ta yi, kafin wani irin farin ciki ya shiga mamaye kirjinta tamkar yanzu ne ta ji Taufeek zai iya sama mata jika Da sauri ta ce" Mamansu kina nufin ciki ne da KHausar?" Mama ta yi murmushi cike da kunya ta ce" Kai Mamansu Allah ya bamu ALKHAIRI Ni dai na kashe" Daga nan ta kashe, ita kuma Mama sai ta kasa ci gaba da aikin nata karshema fitowa ta yi ta dauki hijab din ta ta zumbula ta fice da nufin zuwa ta ga ko sun dawo, Duda tunda suka yi kaurar zuwanta daya tak ta saka albarka , sai take ji YANZUN ba zata iya hakura ba sai ta je ta ganta inma da hali a je asibitin nan yanzu, dan in zata irga da kyau KHausar ta jima cikin juwar nan, hakan na nufin ta wuce watannin da ya dace ace ta fara awo fatanta Allah ya sa sun dawo Tana kokarin karasawa wajen kofar Muryar HAJIA dake rike da leda baka shake da kayan turare turarenta , Hamdiya rike da katon kaskon wutar ta ce" Wace wannan kamar matar mai kwanoni zata je bangaren sirikai" Tsam ta yi tana zarro ido, sai kuma ta juyo tana murmushi hadi da sosa keya cike da jin kunya ta ce" Lah HAJIA ina yini, dama dama zan leka ne na ga wai ko KHausar din na nan?" Hajia ta saki murmushi ta ce" Ki ji tsoron mai sama, ba ta zo ta mana Salama ba? Kar ki dauki hali irin nawa kulun ina bangarenku, iyi sirikan zaki sakawa ido? Koda yake gwara in San na bar baya gwara ki fara zuwan kar Na mutu na bar marayan Allah yan uba su ga bayansa, kama ledar mu je in fada maki kowane amfaninsa " Mama ta ce" 💔💔💔💔❤‍🩹❤‍🩹💔💔💔💔 *DA CIWO A ZUCIYATA* 💔💔💔💔❤‍🩹❤‍🩹💔💔💔💔 _MALLAKIN_ *SAJIDA NIJAR* *FREE BOOK NE* 6️⃣3️⃣ *GARABASA, GARABASA, PROMOTION, PROMOTION DIN LITATAFAN MARUBUCIYAR A KAN FARASHI MAI SAUKI 1K, YAN NIJAR KUWA 1000 FRANCS CEFA* 1: Duk karyar kada 2: Yar mahaukaciya 3: Neman na kaina 4: Bani da zabi 5: Bak'a ce 6: Kutkale 7: Makauniya ce 8: Mage 9: Duk nisan jifa 10: Idan ka raina inda kake 11: Dutse 12: Alkalamin kadarata 13: Bani da zabi 14: Dakika Biyar 15:Wata kokowar 16: Aure yakin mata 17: Ni zan ladabi 18: Daga tafia daukar soja *Dukansu a kan farashi mai sauki, zaka saka dubu guda ne domin promotion ne nake yi, ka tuntubeni kan layina kamar haka +227 93 81 16 18, Sajida Nijar* Now *Da CIWO A ZUCIYATA* *Tallah, tallah, tallah* *SECRET DE LA FEMME DU MANGA* _Gidan Kamshi, Sirrin Manyan Mata, nesa tazo kusa,Amarya ,Uwar gida,Ango da mai gida Har ma da yan mata da samari shin kuna sane da cewa HAJIYA FUSAM ta shirya tsaf domin gwangwaje ku da turarakunta masu dankaran kamshi? Tare Kayan gyaram jiki na musamman ,wanda daga nesa kamshin ki kadai ya wadatar ya isar da sakon zuwanki waje,gidan ki kuwa sai ya zam abun kwatance wajen kamshi, kar na cika ku da surutu bara in fara zayyano su_ Farar Humura Bakar Humura Humura special, humura de bain Humura epicé Lait de nuit Parfums désodorisant Parfums rideau et dras Lait de nuit Alkam Kulakcam *Waɗannan kadan ne daga bangaren turaran ruwa* Gagab, sandal flex, Durot, durus, sandal fleur, tafarce, farce, sandal bangui, sandal, hypotonic sandal, al'ut, coktail creation VIP, Gajiji, Mankaji, turaran wutar labule da cafet, Aba malan, boulettes *Munada bangaren gyaran jiki kamar haka:* mai mai saka santsin jiki, mai mai kanshi, Kayan gyaran jiki mai saka fata ta yi santsi da laushi, kayan gyaran jiki mai saka fata ta yi fari, Sabulu mai saka fata ta yi haske, sabulu mai saka fata ta yi santsi, sabulu mai goge yanayin fata, mai wanda baya saka fari mai gyara fata Sayen na gari mai da kudi gida,sai an gwada akan san na kwarai💃💃 Hajiya Fusam na zaune a kasar Niger domin yin magana da ita kai tsaye tuntuɓi wannan number 97 82 44 94 *SECRET DE LA FEMME DU MANGA* Gidan Kamshi, Sirrin Manyan Mata💃💃💃💃💃 Tallah 3 Hajiata, ke kin san rayuwar aure sai da anini, in babu jagab a babar eriya oga ya kama tofa yawu da neman yadda zai yi bawan Allah, idan kuma babar haja a bude ham ai ba labari oga sai dai ya shiga ya fito kamar ya shiga kofar ruwa😔, zo ki ji, a farashi mai rahusa zaki gwangwaje ki rike bakin Elhaji gudun tada yara, ama idan lamari ya yi lamari tsaf zaku karya gado☹️🫣 🔥💥🔥💥🔥💥🔥💥🔥💥🔥💥🔥💥 *HOHOHO WANI KAYA SAI AMALE, DON JAKI BAZAI 'DAUKA BA, INA MATA MASU BUK'ATAR 'DAGA DARAJARSU A WAJAN MAZAJENSU INA MATAN DAKE SHAN WULAK'ANCIN MIJI KO NA KISHIYA ,INA MATAN DAKESON ZAMOWA MOWA AGIDAJEN AURENSU TO ALBISHINRU MAMAN ZARAH YAR MUTAN SOKOTO TA SHIRYA TSAF DOMIN GABATAR MAKU DA ZAFAFAN KAYAN MATA MASU KYAU DA INGANCI WANDA BASUDA ALGUS ACIKI , AKWAI MAGANI DANAYI BINCIKE AKANSU DAN FARIN CIKIN MA'AURATA NAMU BA IRIN NASU BANE KAYAN MU NA DABAN NE NA ASALIN SAKKWATAWAN SHEHU MASU ABUN MAMAKI* 07034251528 kayanmu masu inganci ne masu ladaftar da kowane irin namiji Kad'an daga cikin abubuwan da muke dasu Ingantaccen maganin nono , Wanda zai gyara maki nononki donmin dawo da martaban nononki acikin kankanin lokaci komai lalacewarshi kuwa sauran bayani sai mun had'u pc +234 703 425 1528 Maganin hips (hips up) Wanda zai ciko maki da hips dinki su cika suyi bul bul ga laushi dasu k'ara suyi dass abun sha'awar kowane namiji Maganin infection Sha yanzu magani yanzu Yana fatattakar sanyi cikin kankanin lokaci magani ne na maza da Mata insha Allah kowane irin sanyi gareki kikayi amfani dasu anwuce wajan Ingantacce Kuma sahihin maganin k'iba Wanda Zaki ciko acik kankanin lokaci zakiyi kibar ki Yar dai dai misali ki huta Zama da Rama Baki rasa ci ba Baki rasa sha ba amma kullum Ana kallon cewa kinada matsala agidan aurenki saboda wannan ramar , Rama batayi ba Sam Yar uwa Sabulun wanka Kalolin sabulun tsarki Turaren tsugunno Turaren al'ajab Hatsabibin turare Da sauransu 07034251528 Kalolin gumba Gumbar Dabino Gumbar gero Gumbar madara Gumbar matsi Gumbar ukku bala'i Gumbar tada zaune tsaye Gumbar sabon budurci Gumbar sa buzu kuwa Gumbar aya da kwakwa Gumbar ridi Gumbar mazari Sarauniyar gumba 3in1 Da sauran kalolin da bansamu fadi ba, Kalolin gari Garin mallaka Garin hutar da malaminki dakan jaraba Dakan Amare Dakan Ni'ima Dakan kishiya in bakiyi bani waje Garin sa buzu kuwa Garin buje.sharkaf Garin Dan la'asar Yayan hadiya mai suna dan la'asar Original Dan goshi Original Dan goshi (sabon salo) Original man damo Original man ayu Kitsen damo Sirrin tafin kafa Sirrin farinjini na uwargida da amarya harma da yan mata Kwallin idonka idona Muna hada set na sirrin mallaka hajiya ba boka ba Mallam sai tarin sirrika kema kizama kowa agidan surenki Akwai hadin sabon budurci ga yarinyar data rasa budurcinta ta hanyar fyade ko yaudarar d'a namiji da izinin Allah akayi maki wannan hadin to an wuce wajan sauaran bayani sai mun had'u pc Kalolin tsumi Tsumin mallaka Tsumin jaraba Tsumin madarar ni'ima Tsumin tabaje Tsumin Amare Tsumin sabon budurci Tsumin nono rakumi Matan gaske Ruwan jaraba, Da sauran kalolin da ban fada ba Kalolin matsi da basuda illa ajikin mace sai dai ma sukara maki lafiyar Matsin Dan mannau Matsin mallaka Dan la'asar Sabon budurci Mak'alemata Mashahurin matsi Ukku bala'i Matsin uban budurwa Akwai gumba ta matsi wadda Shanta akeyi ga matan da basa son yin matsi Muna hada set ga wadda Allah ya jaranfa da matsalar fyade har yarasa budurcinta , muna hada mata kaya ingantattun don dawo da martabar ta, Hohohohoho in ana dara fidda uwa ake *Kyallen al'ajabi* babban sirrin mallaka mai abun al'ajabi mallaki naki don samun damar shiga cikin jerin mata masu fada aji a gidan mazajensu , KARKU manta da sunan maman zarah sokoto sayen nagari maida kudi gida 07034251528 ina maraba daku sayen daya ko sari ina Sokoto sannan ina aikawa kowane gari cikin aminci da yardar Allah Ga Wanda suke bukatar ganin kalolin kayana to suyi sarving number na suyimun magana nayi sarving number ku zaku dinga ganin kalolin kayana a status ngd sosai 07034251528 Maman zarah mabera SOKOTO Mama ta ce" A'a HAJIA Bara na juya " HAJIA ta kama hannunta ta saka mata ledar ta yi gaba tana fada da fadin" Aikin banza da na mutu na san da tuni an rabata da mijin tana abu kamar wata wace ta zauna gidan kanwarta , shirme da suka tada rigimar gida in ba dan nace zan dagawa uban kowa nono ba har ta wani ce a bar gidan ita ga wace bata son rigima, Ni ina so kuma du wanda ya dagawa magidanci hankali shi Bama dan balaja'u bane!" Ita dai Mama sai ta ji kunya gaba daya ta hannata sukuni Sunna shiga suka tarar da KHausar ta juye hantar nan a plate ta gyara zama saman cafet ta fara ci ta dago tana sakin murmushi da amsa sakamar HAJIA sai kuma ta ga harda mama dan haka sai ta mike gaba daya tana masu sannu ta dauko abinda take dora kaskon HAJIA saboda abin garwashin kar ya zuzube sannan ta je ta dibo masu ruwa ta kawo masu da jus ta zauna tana gaishe su HAJIA ta mika hannu ta dauko plate din ta dauki daya ta dangwala yaji zata Kai baki TAUFEEK ya sauko daga sama , Allah ya taimake shi da jalabiya a jikinsa ya nufo falon yana jin HAJIA ta ce" Yanzu Khausara abinda zaki ci ki barni Kennan bayan kin ga ba jinnin kirki ne da Ni ba?" KHausar ta janyo ledar tana fadin" HAJIA kin ga naki nan, biyu na raba dama na daure naki a leda, yinwa ce ta hannani zuwa na kai nace bari na ci sai na kai" Plate din ya karbe yana sakar mata harara ya ce" An ki ba'a bakin, ke kam gaskiya ki daina zuwar min kina saka min mata a gaba kina hannata ci ta murmuje wannan ai harda daukan alhaki kamar da kudinki aka siyo?" HAJIA ta kalli Mama ta ce" Ai sai ki amso min ko? Kina kallo d'anki zai min rashin kunya shi algungumi!, Ke Hamadiya je daukon ta ledar , Allah ya taimakeni Khausara na kaunata duk wani wanda baya so sai ya rintse idonsa, yar nan du abinda ta kai bakanta sai ta kai min na kai, har tashina take tana cusan kaza a baki, da babu ita ai da na mutu yanzu, kina gannin tunda Magidanci ya aurota nake Kumari kumatuna sunna dawowa?" Mama ta sakar masa harara ta ce" Kai, ajiye" Murmushi ya yi ya karasa daf da HAJIA ya ajiye plate din HAJIA ta zazage sauran hantar ta zauna daf da KHausar suka saka KHausar din a tsakiya ta ce" Saka hannu mu ci, bismilanku ama kar a wuce bibiyu dan Allah, ke Hamadiya karbi nan saka a salatinki maza ki koma wajen uwar rikonki kar ta tsine maki saboda Ni" Hamdiya ta mike jiki ba karfi ta amsa ta juya ta tafi tana share hawaye, dama ta yi nacin biyo HAJIA ne dan ta san idan har bata ganshi ba yau ta yiwu ita da shi sai a lahira in ana haduwa, Shikenan saboda ta sanarwa mama dan Allah sadakinta da akace za'a kawo gidan iyayenta kar a amsa ita ƴaƴansu take so shine ta yi mata dukan Kawo wuka sannan tace zata bar garin a satin nan, ya Allah ita ta san son shi sai ya kasheta Mama ta rasa ta inda zata bilowa magamar, gashi abin ya tsaye mata a rai sosai ta kasa tashi ta tafi, tana zaune ne HAJIA na cin hantarta da ta kasa tana ta labari , Khausar din na rike da plate din Ajiyar zuciya Maman ta sauke bayan ta dan yi wani tunani ta ce" KHausar, Ni da kika yi gwajin abinda ke saka ki juwar nan me aka gani?" KHausar ta kalli Mama tana sauke numfashi ta ce" Ba'a ga komai ba Mama, hatta bugun zuciyata daidai ne" HAJIA ta ce" Me kuwa za'a gani Allah na tuba , na fada maki a ringa kula da magauta bakya ji, in sha Allah sai na maidawa mai neman Khausara da balaki aniyarsa, da Dije ake zance!" TAUFEEK ya karbe hantar da ta dauko cikin kason KHausar ya mayarwa KHausar din ya karbe plate din yana sakar mata harara ya ce" Mama, Ni abin nan zan aunata da kaina gobe in sha Allah, ina kyautata zaton bata wani je wajen docter ba dan ba son allura take yi ba" Mama dake kauda kai ta ce" Ok, Allah ya nuna mana, ama ka yi mata harda pregnancy test " Da sauri ya juyo daga barin HAJIA dake son karbe hantar ya zubawa Mama ido, itama KHausar sai ta samu kanta da zubama Mama ido jin abinda Maman ta ce, ita kuma Mama sai ta mike tana alamun tafiya zata yi HAJIA ta mike ta karbi plate din tana fadin" Yau ga bakin ciki, sai na ci, ke minene shi prcy taste din?" Mama ta yi turus , ta juyo ta zubawa HAJIA ido, gannin itama amsa take so sai ta dan sosa goshinta ta ce" Dama, Mamansu KHausar ce ta yi kirana dazu tace juwar nan ta KHausar a duba ta yiwu wata kama ce" "Ki rantse da huwa rahamanu, Kina nufin Juwar da y'ar nan ke yi ko sati bata cika a gidan nan a matsayin matar MAGIDANCI juwar ciki ce? La'ila ha ilalahu Muhammadu rasululahi sallalahu alaihi Wasallam, wayo Ni Dije Allah na gode maka , ke ama tsaya yo wani irin ciki kuma? A irgena ai ta yi wata bakwai a gidan nan ga ciki shafe kamar nawa ? Ke dan mike dan mutun ai ya fi karfin kwonciya a mara ko? Dan mike in gani , kar dai yar nan irin matan nan ne da ciki ke shigewa nono da duwawu, tashi in gani sun karu ne ko mene? Yau na ga ikon Allah Ni Dije, yanzu ciki ne da ke?" HAJIA ke fada tana salalami, Mama ta yi saurin ficewa ya zamto sai TAUFEEK din da KHausar da HAJIA, sunna bin hajiar da kallo tamkar bakuwar halitta TAUFEEK ya lumshe idannuwansa da kyar, a hankali ya ce" HAJIA barta dan Allah kar ki dagata da karfi mana kin ce a cinya in fa kika daki kan dan ko yar a cinyar nata?" HAJIA ta saki KHausar ta dan matsa daf da shi ta ce" Kuma fa hakane, to ama kai likita ita likita karatun jabo ne kuka karanta da zaka dirkawa yar mutane ciki ana ce min juwa take? Wannan ai wulakanci ne, Magidanci ka yiwa Allah ka tashi mu je a tabbatar min da cikin nan ko na iya rintsawa, wayo Allah mai alheri ashe ashe abin a kusa yake, kai ana iya shege kace na maka auren dole?" A raunane ya sake duban HAJIA a fizge ya ce" Tashi ki je bangarenki kin ji kakata?" HAJIA ta sakar masa harara ta dauke kai ta ce" Aikin birit in ji tusa ai ko tsohon mutun yau ba zai rabani da KHausara ba, kin ga cinye hantar kin ji? Baiwar Allah ashe yan kwadayin da na fara tsorata na ALKHAIRI ne?, In me ta sameni ina ci yar nan sai ta ci shi har na fara tsorata ashe ashe ashe asusun Magidanci ke habaka? Ka tashi mu je!" Ta idasa fada da dan karfi tana wartar kaskon wutar nan ta ce" Bari in kai raushin in zo, dauko mata sutura mu je!" HAJIA na fita ya samu ya kamo hannayenta yana sake tsatsareta da ido A hankali ya ce," Dan Allah fada min haka ne? Are you pregnant?, KHausar tunda muka zama abu daya da kwana uku kika fara juwar nan, tl me please Akoy babyna a nan?" Cike da kunya KHausar ta sada kanta tana janye hannunta , gaba daya ta shiga a halin rudu Taufeek ya sake janyota jikinsa sosai yana dage rigarta a tausashe ya ce" Kar ki sako kunyar nan yanzu, na fi so na gane eh ne ko a'a? Ina son ganewa" Ajiyar zuciya ta sauke, ta rasa ita amsar da zata bashi, abinda ta sani shine kwarai lokuta da dama idan mahaifiyarta ta tsananta juwa kwanaki ƙalilan tsakani zata tashi da nakuda ne, ama shin itama irinta ne ko yayane?, Ita dai bata sani ba, kuma shima ta tabbata ya shiga rudani ne na tunanin maganar nan, ko dan shi din likitan kwakwaluwa ne ba na mata ba? Ama koda likitan kwakwaluwa ne yanada wasu sani a fanin matan, shine zai fada mata ai ba ita ba, A sanyaye bayan ta kama hannun nasa itama ta ce" TAUFEEK ban sani ba, ban sani ba, Ni dai na san ina juwa, ina cin abinci fiye da da, wani lokacin kuma nakan ji gajiya sosai ama da zarar na yi barci Shikenan sai ka ga komai ya wuce" Zai kuma yin magana wayarsa ta ringa ringing sosai a dole ya dauko ya daga bayan ya ga mamansa ne Da wata Muryar da maman bata cika amfani da ita ba ta ce" TAUFEEK dama Yumnah nakuda take yi tunda yama ban sani ba?" A hankali ya samu kansa da lumshe ido, a Nutse ya ce" Nakuda?, Ban je part dinta ba , tana wajenku ne?" Mama ta furzar da hucin bacin rai , ta cire hijab dinta ta ce" Ni na isa na san abinda take ciki ko na kai matsayin sani? TAUFEEK ace ina cikin gidan nan da raina da lafiyata ka auro macen da zata raina Ni? Tun ban yarda na furta ba har ta kaini makura? Ni makiyiyarta ce ko bata san girman mahaifiyarta ba da zata raina Ni?, Ace ina cikin gidan nan jikinta ya motsa na abin dake cikinta wanda nake cikin zumudin zuwansa duniya nake siye siye dominsa nake addu'a ba dare ba rana kan Allah ya nuna min, sai yanzu HAJIA nawarah ta shigo ta fada min cewa wai tunda yama sunna tare da mahaifiyar Yumnah a bangarenta tana kan gwuiwa YANZUN dai jikin ya motsa sosai ta yiwu haihuwar ce in sanar maka zasu tafi asibiti? Na nuna a kan me ba'a sanar min ba tace wai Yumnar ce bata so KHausar ta san tana nakuda sai dai ta ganta da abinda ta haifa? Wannan wace irin masifafiyar nataciyar gaba ce yarinyar nan ke fama da ita a ranta tana tare da yan zuga?, To bari ka ji, ina fatan matarka ta sauka lafiya, ama ka sani na kai makura , tunda har Ni Khadija ban isa da ita ba ba laifi Allah ya raya , ama Nima babu ruwana da dukkan abinda ya shafeta , ciki harda abinda zata haifa!" Daga haka Mama ta katse kiranta ta jefar da wayar ta yi zaune a bakin gadonta tana dafe kanta wasu hawaye Masu zafi suka balo mata Shin yaushe ne zata samu sasaucin zama da abokanan zamanta? Ko dai har ta koma ga Ubangijinta ba ranar samun sauki? Tun bata saba wahalaliyar raayuwar nan ba har ta gane in fa ba kanta ta rike ba komai na iya faruwa ciki harda sakwantar mata da cilon danta, sai ta basu lafiya take rayuwarta a gefe itama Ama abu kulun cikin tugu da shari kala kala ake yi mata? Tun tana da jan sawunta har yanzu da jinni ya dauke mata take kokowa da su da lamarinsu, shin yaushe zasu bata lafiya? Ace matar TAUFEEK, TAUFEEK nata , sai dai ta hangota da su? Me take tunani ne ita Yumnar?, Ba damuwa ko TAUFEEK suka kwace zata yi addu'a ta bishi da addu'a bale wata Yumnar banza da wofi, Allah ya taimaketa ga KHausar, wace ta mayar da ita tamkar uwar da ta haifeta, tunda ya auri KHausar take rayuwa da yanci itama a cikin gidan, take da abokiyar fira, mai yi mata girki ta kawo mata, mai zuwa ta yi mata fira, mai share mata kaso tamanin a damuwarta, kuma ga kyautar Allah ya bata itama, in sha Allah zata kaita asibiti da kanta gobe da safe a duba mata ita, su dawo ta raini cikin nan dan ba zata yarda ta koma aiki ba sai ta haihu da izinin ubangiji A kalla ta dauki minti ashirin a zaunen nan tana share hawaye ta ringa jiyo hayaniya sama kamar za'a tsaga falon nasu Sai da ta Saurara sannan ta ji gabanta ya fadi, ba dan komai ba sai dan tunawa da ta yi waye danta da tsinkayo muryarsa da ta yi sama da ta kowa, da Muryar kakarsa na dafe masa baya sai uwa uba Muryar mahaifinsa A dole ta saka hijab dinta ta fito sanan ta nufi kasan tana kallon taron ba laifi harda maman Yumnah da yayarta da kuma Yumnar dake murkususu ko yaya aka yi aka nufo nan da ita kuma? Mai kwanoni ne ya sauke ajiyar zuciya dan ya san yanzu rigimar ta lafa tunda wace ake rikicin kanta ta sauko, ya kuma san ita din mai hakuri da sanyaya fitina ce da KOWAMA bale in ta ga abin ya shafe shi, sai ya sauke ajiyar zuciya a karro na ba adadi ya ce" Maman Magidanci, ai gwara da kika sauko, shin ko me ya bata masa rai ai yana iya yin hakuri har wannan taa samu lafiya , haihuwa ai ba wasa ba maman Magidanci , sun fito zasu shiga Mota su nufi asibiti wai ya tarda su yace idan aka fita da ita a bakin aurenta sai kace ba likita ba? Kuma na yi tsawar kin ga HAJIA a gefe kin san dai ba barina zata yi in Hanna ba, dan Allah a yi hakuri a yayafawa matsalar ruwan sanyi, komai ya yi zafi maganinsa Allah, kuma hakuri shine ja gaban komai a rayuwa kin ji maman mai kwanoni?" (Wato ashe da baya kiran sunnanta dan fa ci sunan HAJIA ne?) Mama ta kai dubanta kan KHausar wace mahaifiyarta ke sake talabarta dan ko tsayawa ta kasa yi, da gaske haihuwa ta zo mata dan kiris ya rage dan du ta fita hayacinta kukanma ya dauke azaba ta yi azaba kuma ga abinda mijinta yace Mama ta ce" Elhaji a kaita asibiti mana, sannu Allah ya raba lafiya" Daga haka maman ta juya da nufin komawa Da mamaki ya ce" A'a, yaya zaki ce haka ki juya , wai yaya zaku tsaya wasa da haihuwa ne? Ke ku kamata a kaita asibiti" ya fada yana duban su KHausar dake tsatsaye, domin a lokacin da TAUFEEK ya maka wayar da suka yi da Mama a kas ya fice bai ce da ita ufan ba ta fito a guje ta bi bayansa tana ihun lafiya? Sai ta ga ya nufi bangaren Yumnah, da farko ta so komawa sai sai sunna tunkara ta ga an talabo Yumnar, a dole ta karasa tana aukin sannu, sai dai abinda ya fada ya saka su Dukansu rikicewa a lokacin da TAUFEEK, professeur TAUFEEK ya dubi tsabar idannuwan MACEN dake kan gwuiwa matarsa yace idan har aka fita da ita a bakin aurenta, sannan ya dubi mahaifiyarta yace da ita babu wanda ya isa ya wulakanta min uwata in ga darajarsa a duniya ko waye, sai kuma ya kalli HAJIA nawarah wace ta fara sarewa yace da ita a yau a gidan nan ko Ni ko ke, sai suka idasa sarewa duniya baki dayansu HAJIA ce ta yi gagawar fadin" A kama wace? Sunna da damar tafiya da ita ama ka ji ai abinda mijinta yace , duk shegiyar da ta isa ta fita da ita a bakacin aurenta!" Da mamaki Mai kwanoni ya sake yinkurawa zai yi wata maganar da tsawa da kuma rarashi da fadan a yi maza a kai baiwar Allah asibiti sai Yumnah ta yi wani irin ihu da nishi wanda ke nuni du inda kan d'a yake yana daf da zuwa duniya A rikice suka rikice, gasu a falo su duka, Mama tuni ta komawarta dakinta ta datse da ky dan ta san mai kwanoni na iya cenza mata ra'ayi YANZUN nan, ita kuma ta yi rantsuwa babu ruwanta, abin ya isa haka, iskancin ya kai wajen da ba zata iya dauka ba kuma! Kiri kiri TAUFEEK ya yi tsaye kikam a lokacinda KHausar ke sake sakin nishimai tare da bayanin fitowar kan Da daga jikinta Da sauri mai kwanoni ya fice, kusan suka fita tare shi da KHausar wace ta yi bangarenta da gudu ta warto Safar hannu da kayan aikinta ta juyo da gudu gudu tana saka Safar hannun ta koma dakin hankalinta tashe , kana ganninta ka san taimako ne zata bada dan ceton rai Wato an yi gudun Gara an fada gidan zago, sai ga KHausar din da aka so sai an haihu ta ji duke gaban Yumnah ƙafafuwan Yumnah Ware a irin mummunar warewa, jikinta bude a budewar da ko mijinta da wahala in ya taba gani a zamantakewarsu, jiki ya aune halitta ta zazago ta bude kai ya bado tana ihun azaba da ni'imar ubangiji har kai ya fito KHausar ta kama cikin kwarewa na cikakkiyar likita mai ruwa da tsaki a fannin amsar haihuwa ta juya jikin baby cikin dabara ta fitar da hannu daya sannan ta sake juyawa ta fitar da dayan kafin ta janyo babyn da ta tsalara kuka kamar a baakinta aka fara gwajin kukan, ta mike ta mikawa Aunty Akilah dake hawaye, hawayen girma irin na hukuncin ubangiji wanda ya fi kowa tsara komai, wannan shine kana naka Allah na nashi,daga wannan idan mahaifiyarsu da kanwarta suka ci gaba da wani abin to lalle zata dage da sanarwa ubangiji kan ya shirye su baki daya, a raunane ta sake kallon mijin kanwar nata wanda ya juya ya fice a lokacin da aka shiga musayar yawun ta karu, sai an yi mata ɗinki, gashi ya Hanna fitar, wannan shine ga koshi ga kwanan yinwa , ga amsar haihuwa daga wajen kishiya ga kuma ɗinki da kishiyar zata mata......... *ASALAMU ALAIKUM WA RAHAMATULAH YAN UWA, SAKWANI NA SAMUNA SOSAI TA MAGANA KAN TALLAH DA NA SAKA , ANA CEWA TA YI YAWA, HAKANE KAM TALLAH NA SAKATA SOSAI MASHA ALLAH, A HAKAMA NA RUFE AMSA NE , KU YI HAKURI TALLAR NAN DA KUDI NE NAKE YINTA😂🥹 , ama idan da wace zata maida masu kudadensu sai na bayar da account numba a maida masu sai na daina sakawa in sha Allah, daya ta biya Ni a kudinmu na Nijar jaka arba'in, dayar kuwa ta saka dubu goma dan mutunci, na gode😍😍😍😍😍😍😍😍* 💔💔💔💔❤‍🩹❤‍🩹💔💔💔💔 *DA CIWO A ZUCIYATA* 💔💔💔💔❤‍🩹❤‍🩹💔💔💔💔 _MALLAKIN_ *SAJIDA NIJAR* *FREE BOOK NE* 6️⃣4️⃣ *GARABASA, GARABASA, PROMOTION, PROMOTION DIN LITATAFAN MARUBUCIYAR A KAN FARASHI MAI SAUKI 1K, YAN NIJAR KUWA 1000 FRANCS CEFA* 1: Duk karyar kada 2: Yar mahaukaciya 3: Neman na kaina 4: Bani da zabi 5: Bak'a ce 6: Kutkale 7: Makauniya ce 8: Mage 9: Duk nisan jifa 10: Idan ka raina inda kake 11: Dutse 12: Alkalamin kadarata 13: Bani da zabi 14: Dakika Biyar 15:Wata kokowar 16: Aure yakin mata 17: Ni zan ladabi 18: Daga tafia daukar soja *Dukansu a kan farashi mai sauki, zaka saka dubu guda ne domin promotion ne nake yi, ka tuntubeni kan layina kamar haka +227 93 81 16 18, Sajida Nijar* Now *Da CIWO A ZUCIYATA* *Tallah, tallah, tallah* *SECRET DE LA FEMME DU MANGA* _Gidan Kamshi, Sirrin Manyan Mata, nesa tazo kusa,Amarya ,Uwar gida,Ango da mai gida Har ma da yan mata da samari shin kuna sane da cewa HAJIYA FUSAM ta shirya tsaf domin gwangwaje ku da turarakunta masu dankaran kamshi? Tare Kayan gyaram jiki na musamman ,wanda daga nesa kamshin ki kadai ya wadatar ya isar da sakon zuwanki waje,gidan ki kuwa sai ya zam abun kwatance wajen kamshi, kar na cika ku da surutu bara in fara zayyano su_ Farar Humura Bakar Humura Humura special, humura de bain Humura epicé Lait de nuit Parfums désodorisant Parfums rideau et dras Lait de nuit Alkam Kulakcam *Waɗannan kadan ne daga bangaren turaran ruwa* Gagab, sandal flex, Durot, durus, sandal fleur, tafarce, farce, sandal bangui, sandal, hypotonic sandal, al'ut, coktail creation VIP, Gajiji, Mankaji, turaran wutar labule da cafet, Aba malan, boulettes *Munada bangaren gyaran jiki kamar haka:* mai mai saka santsin jiki, mai mai kanshi, Kayan gyaran jiki mai saka fata ta yi santsi da laushi, kayan gyaran jiki mai saka fata ta yi fari, Sabulu mai saka fata ta yi haske, sabulu mai saka fata ta yi santsi, sabulu mai goge yanayin fata, mai wanda baya saka fari mai gyara fata Sayen na gari mai da kudi gida,sai an gwada akan san na kwarai💃💃 Hajiya Fusam na zaune a kasar Niger domin yin magana da ita kai tsaye tuntuɓi wannan number 97 82 44 94 *SECRET DE LA FEMME DU MANGA* Gidan Kamshi, Sirrin Manyan Mata💃💃💃💃💃 Tallah 3 Hajiata, ke kin san rayuwar aure sai da anini, in babu jagab a babar eriya oga ya kama tofa yawu da neman yadda zai yi bawan Allah, idan kuma babar haja a bude ham ai ba labari oga sai dai ya shiga ya fito kamar ya shiga kofar ruwa😔, zo ki ji, a farashi mai rahusa zaki gwangwaje ki rike bakin Elhaji gudun tada yara, ama idan lamari ya yi lamari tsaf zaku karya gado☹️🫣 🔥💥🔥💥🔥💥🔥💥🔥💥🔥💥🔥💥 *HOHOHO WANI KAYA SAI AMALE, DON JAKI BAZAI 'DAUKA BA, INA MATA MASU BUK'ATAR 'DAGA DARAJARSU A WAJAN MAZAJENSU INA MATAN DAKE SHAN WULAK'ANCIN MIJI KO NA KISHIYA ,INA MATAN DAKESON ZAMOWA MOWA AGIDAJEN AURENSU TO ALBISHINRU MAMAN ZARAH YAR MUTAN SOKOTO TA SHIRYA TSAF DOMIN GABATAR MAKU DA ZAFAFAN KAYAN MATA MASU KYAU DA INGANCI WANDA BASUDA ALGUS ACIKI , AKWAI MAGANI DANAYI BINCIKE AKANSU DAN FARIN CIKIN MA'AURATA NAMU BA IRIN NASU BANE KAYAN MU NA DABAN NE NA ASALIN SAKKWATAWAN SHEHU MASU ABUN MAMAKI* 07034251528 kayanmu masu inganci ne masu ladaftar da kowane irin namiji Kad'an daga cikin abubuwan da muke dasu Ingantaccen maganin nono , Wanda zai gyara maki nononki donmin dawo da martaban nononki acikin kankanin lokaci komai lalacewarshi kuwa sauran bayani sai mun had'u pc +234 703 425 1528 Maganin hips (hips up) Wanda zai ciko maki da hips dinki su cika suyi bul bul ga laushi dasu k'ara suyi dass abun sha'awar kowane namiji Maganin infection Sha yanzu magani yanzu Yana fatattakar sanyi cikin kankanin lokaci magani ne na maza da Mata insha Allah kowane irin sanyi gareki kikayi amfani dasu anwuce wajan Ingantacce Kuma sahihin maganin k'iba Wanda Zaki ciko acik kankanin lokaci zakiyi kibar ki Yar dai dai misali ki huta Zama da Rama Baki rasa ci ba Baki rasa sha ba amma kullum Ana kallon cewa kinada matsala agidan aurenki saboda wannan ramar , Rama batayi ba Sam Yar uwa Sabulun wanka Kalolin sabulun tsarki Turaren tsugunno Turaren al'ajab Hatsabibin turare Da sauransu 07034251528 Kalolin gumba Gumbar Dabino Gumbar gero Gumbar madara Gumbar matsi Gumbar ukku bala'i Gumbar tada zaune tsaye Gumbar sabon budurci Gumbar sa buzu kuwa Gumbar aya da kwakwa Gumbar ridi Gumbar mazari Sarauniyar gumba 3in1 Da sauran kalolin da bansamu fadi ba, Kalolin gari Garin mallaka Garin hutar da malaminki dakan jaraba Dakan Amare Dakan Ni'ima Dakan kishiya in bakiyi bani waje Garin sa buzu kuwa Garin buje.sharkaf Garin Dan la'asar Yayan hadiya mai suna dan la'asar Original Dan goshi Original Dan goshi (sabon salo) Original man damo Original man ayu Kitsen damo Sirrin tafin kafa Sirrin farinjini na uwargida da amarya harma da yan mata Kwallin idonka idona Muna hada set na sirrin mallaka hajiya ba boka ba Mallam sai tarin sirrika kema kizama kowa agidan surenki Akwai hadin sabon budurci ga yarinyar data rasa budurcinta ta hanyar fyade ko yaudarar d'a namiji da izinin Allah akayi maki wannan hadin to an wuce wajan sauaran bayani sai mun had'u pc Kalolin tsumi Tsumin mallaka Tsumin jaraba Tsumin madarar ni'ima Tsumin tabaje Tsumin Amare Tsumin sabon budurci Tsumin nono rakumi Matan gaske Ruwan jaraba, Da sauran kalolin da ban fada ba Kalolin matsi da basuda illa ajikin mace sai dai ma sukara maki lafiyar Matsin Dan mannau Matsin mallaka Dan la'asar Sabon budurci Mak'alemata Mashahurin matsi Ukku bala'i Matsin uban budurwa Akwai gumba ta matsi wadda Shanta akeyi ga matan da basa son yin matsi Muna hada set ga wadda Allah ya jaranfa da matsalar fyade har yarasa budurcinta , muna hada mata kaya ingantattun don dawo da martabar ta, Hohohohoho in ana dara fidda uwa ake *Kyallen al'ajabi* babban sirrin mallaka mai abun al'ajabi mallaki naki don samun damar shiga cikin jerin mata masu fada aji a gidan mazajensu , KARKU manta da sunan maman zarah sokoto sayen nagari maida kudi gida 07034251528 ina maraba daku sayen daya ko sari ina Sokoto sannan ina aikawa kowane gari cikin aminci da yardar Allah Ga Wanda suke bukatar ganin kalolin kayana to suyi sarving number na suyimun magana nayi sarving number ku zaku dinga ganin kalolin kayana a status ngd sosai 07034251528 Maman zarah mabera SOKOTO Ba tare da KHausar ta saka komai a ranta ba, ta haɗa allurar ɗinkin nan ta saka wata Safar ba ta yi kyankyaminta ba, bata yi komai ba ta sake zaunawa ta mika hannu da nufin janye rufar da mahaifiyarta ta yi mata tana share mata hawaye kanta a kirjinta ta yi mata mugun rikon da tabas sai ya tambayeta domin rikon MACEN dake kan gabar haihuwa ai riko ne na neman ceton rai Maman Yumnar ne ta iya tare hannun KHausar tana kallonta ta ce" Me zaki yi mata kuma?" KHausar ta dubi mahaifiyar Yumnah, sosai take gannin tashin hankali da abubuwa a fuskar matar, a sanyaye da kula sosai ta ce" Mama, ta karu ne, zan dinke mata ne" Maman Yumnah ta mayar da rufar ta rufe jikin Yumnar ta ce" Ba sai kin yi ba wannanma an gode" KHausar ta zuba mata ido, sai kuma ta juya bata ce komai ba ta mayar da kayan aikinta ta mike ta dauka ta nufi hanyar ficewa HAJIA dake zaune ta yi kwafa tana gyada kai ta juya da nufin bin KHausar din, sai ta ji kuryar Akilah a sanyaye ta nufota tana kallonta ta shiga miko mata jaririyar dake cikin zani sai ihu take yi ta ce" HAJIA, baki amshi y'ar taki ba, HAJIA baki yiwa yar magidancinki Adu'a da Barka da zuwa duniya ba fa?" HAJIA ta lumshe idannuwanta, du yadda ta so kar a ga kwalarta sai da aka gani, murya a sanyaye sosai tana kallon y'ar da ta ci buri da Adu'ar Allah ya nuna mata ta zo ko ya zo duniya, sai gata ta zo din ama a cikin wannan yanayi, ga dai mafarkinta da adu'arta kan Allah ya nuna mata jinninsa, ya haihun a cikin wannan yannayi Murmushi ta yi tana share kwalar ta dubi Akilah dake hawaye a bayyane ta ce" Allah ya maki albarka jikata, ya kuma shiryi yar uwarki da mahaifiyarta, kin ga Akilah bana gaba da kowa Ni, ama yarinyar da bata ga darajar khadija ba, ai ba zata ga tawa ni Dije kakar TAUFEEK ba, Ni kuma kin ga ba tsohuwar da za'a wulakanta bace, koda yarona da jikana basu san zafina na zan gudu na adana kaina ne a wani waje, sai gashi sunna so na, ina son yarinyar nan kamar raina, ama ba zan tabata ba sai mahaifinta ya taba ta, ki kaima su nawarar su rike mata su mata soyyayar mu gani idan har ta Allah ce zata jima!" Daga haka HAJIA ta yi tafiyarta, ta bar Akilah kamar zata kifa, domin abin nan ita fa yana daga mata hankali fiye da tunani, shin yaya za'a yi ace haihuwar da ake yiwa rububi sunna ji sunna gani sunna neman dakilewa? "Akilah, ki kirawo direba mu kaita asibiti, kin ji ta karu ai" Mamansu ta fada muryarta a sanyaye sosai, ta kasa tsayar da tunaninta matsaya daya, wai da gaske yarinyar da suka gama tsara sai dai ta ga Yumnah da yarta ce ta amshi haihuwarta?, Me mahaifiyarsa take nufi tana kallo sarakuwar a halin nakuda ama sai kace ba musulma ba ta kada kai ta tafiyarta? Maganar TAUFEEK kuwa ita ta fi komai tsaye mata a kirji "Mama, yace idan aka fita da Ni a bakin aurena....." Yumnah ta fada muryarta a sanyaye tamkar wace take daf da summa, domin kana ganninta zaka fahimci bayan tashin hankalin rikici da firgicin haihuwa harda na furucin mijinta ke neman tabbata, du irin zumudi irin na uwa da son ganin abinda ta haifa ita kunnayenta na jiyo mata kukan yar da bata kashewa kowa ba bata birnewa kowa ba ta kasa amsarta ko ta dubeta, ji take yi kamar tana daf da barin duniyar baki daya Bata taba tunani cewa wannan lamari zai juye mata haka ba, yau gata zaune kishiyar da take tunanin ko fatar Mamanta ba zata taba gani ba koda ta haihu ce ta amshi haihuwarta, karshe mijinta da take hangen wannan rana da tunanin irin farin cikin da zai yi na murnar gannin abinda ke cikinta ya juya ya fita bayan ya ji kukan shigowar abinda ta haifa duniya bai ko kali jaririyar ba ya yi tafiyarsa ? Innalilahi Wa inna ilaihi raj'une "Yumnah, ki yi hakuri idan bamu je aka dinke ki ba wajen nan tsami zai yi sai kin wahala sosai koda awa daya ya dauka, an fi so da zafi zafin abin haihuwar nan a dinke , mu tafi" mahaifiyarta da ta kamata sosai ta rungumeta take takawa da ita a hankali Murya na rawa Yumnah ta ce" Mama, TAUFEEK, TAUFEEK bai kalli babynsa ba, bai kalleta ba, Mama ban taba tunanin zai iya yin fushi irin wannan ba, Mama babu inda zan je koda kuwa rubewa zan yi, tunda ya fadi haka ba zan taka kofa ba, idan na mutu ai Shikenan, ko me na masa ai sai ya sasauta min haihuwa fa Mama wayo Allahna " ta karashe tana sake fashewa da wani kukan mai tsananin gaske Akilah dake gaba da babyn nan ta dan dakata har suka tardota suka karasa bangaren na Yumnah sai aukin sannu suke yi mata, hankali tashe mahaifiyarta ta zauna tana cusa hannayenta bibiyu a cikin hijab dinta tana murza goshinta da gashinta tana ji kanta kamar zai buga da ciwo dan tashin hankali kaffafuwanta kuwa ji take yi du mujirya ke jansu kamar ba nasa ba Ya Allah, wannan wace irin masifa ce, shin du tsanar ce ta haifar da haka tsakanin yarta da mijinta ko menene? Me aka yi da zafi da zai yi haka? Akilah na shiga ruwa ta tara mai zafi sosai yadda zata iya saka babyn ta zauna ta wanketa sal , yarinyar sai tsala ihu take ta fito ta kimtsata sannan ta jona wani ruwan mai yawan gaske ta tara shi sosai yana ta tururi ta fito ta samu Yumnah kwonce saman shinfidar da Mamanta ta mata har yanzu ta ki ta cire zanin da ya yi kaca kaca da jinni , fuska daure ta ce" Tashi mu je na maki wanka" Yumnah ta dago tana kallonta , da kyar ta budi baki a raunane ta ce" Aunty, ba zan iya wankan nan ba, dan Allah ki ba TAUFEEK hakuri" Akilah ta daure fuska tana kallonta sosai ta ce" Idan kin kula da jikinki zaki bashi hakurin da kanki, in har ya ga zai iya yafe maki ki ci gaba da raina masa uwa tashi daya zai yafe, kin san ke kika san ciwon taki mahaifiyar shi bai sani ba!" Da mamaki Mamansu dake jijiga babyn take duban Akilah, dan kuwa da wahala ka ga Akilah da magana da dacima bale har haka Ita dinma murya a sanyayen ta ce" yaya zaki ce haka? Wani ya raina masa uwa ne?, haba Akilah hankali zaki daga min bayan kina gannin abinda yake faruwa?" Akilah ta sauke ajiyar zuciya ta kama Yumnah suka nufi bayin Ba sasautawa ta yi mata wankan nan sannan ta tara ruwan masu dumi sosai ta danata ciki, ita kuma ta ringa ihu dan kamar zanta zai fita take ji, sosai wajen ya fara yin tsami sosai da sosai Sai da ta riketa suka fito daga dakin suka samu Mamansu na waya da babansu tana sanar masa ai a gidama ta haihu abinda ya sa bai gansu sun dawo ba bata jin dadi ne zasu shigo komai dare in sha Allah Bude wajen da ta tanadi su audugar mata da pant ta yi ta ciro mata komai sannan ta miko mata ta koma ta zauna nesa da su kadan tana kallon mahaifiyarta ta ce" Yaya za'a ce ba'a wulakanta mahaifiyarsa ba bayan abin a bayyane yake ba a boye ba?, na sha fada mata cewar idan ta yarda TAUFEEK ya kula da wani lamari na rashin da'a da take wanzarwa tsakaninta da mahaifiyarsa baki daya darajar da take tunanin tana da ita a duniyarsa tana iya nema ta rasa, uwa wasa ce?, ta san ciwon nata mahaifiyar ama ta kasa girmama ta mijinta? Ban taba gannin banzan tunani irin naki ba Yumnah, ban taba haduwa da mai taurin kai irinki ba, shigowata kasar nan uku bayan aurenki saboda ke, ama a banza, to zan fada maki magana daya tak, duk wani wanda zai so ki kashe aurenki ki fito ba masoyinki bane, mahaifiyarmu ba zata taba fita daga bayanmu ba, haka Allah ya haliceta idan me muka zo mata da shi tana bayanmu ne, da yawa zasu yi anfani da wannan damar su wulakantaki idan har baki san ciwon kanki ba, wace soyayya ce abokiyar ZAMANTA zata maki wace ta zarce Tata? Kina kallo basa son mijinki wace ke da zasu so ki? Na so ace kin yi wayo kin koma gefe kin kalli fadan da bai shafe ki ba wanda kika tarar ana yi a ahalin mijinki, tsakaninsu, na yi iya yina dan ki gane, ama kika kiya kika rintse ido kike daukan hudubar banza kina yabawa kanki dan a rabaki da kishiya!, su su raba kansu da ita mana? Kin kasa ganewa kansu suke nemawa mafita ta kowace fuska, ga dai haihuwar da ta dace ace zuwa yanzu kina nan tamkar sarauniya an zagayeki yan uwa da aminan arziki ana nan nan da ke, ama cikin ikon Allah halayanki sun saka sai kunshe y'a muke daga mu sai mu kamar y'ar gaba da fatiha!, a yanzu bani da abin ce maki, idan kin yi niya ki nemi mafita tun kafin jikinki ya lalace, dan nama kike kayan banza yanzu zaki rube ki fara wari a Gaza haɗawa a dinke a yi biyu babu, babu kyan wannan waje ai kin san TAUFEEK ba zai zauna da ke ba koda kece autar matan duniya!" Tana gama fada da wani bacin ran ta je ta karbi babyn ta wuce ta dauki zamzam da dabino ta wuce ta sauka falon kasa da ita tana jijigata tana tauna mata dabinon da niyar ciyar da ita da shi da kuma ruwan zamzam ranta a mugun bacen da ta jima bata shiga irin halin damuwa saboda bacin rai irin haka ba Kwarai mahaifiyarta ta fi jin Yaren Akilah fiyema da ita, a tsaye take tana rarabawa kanta tunani da neman mafita a zuciyyarta, ga kuma mijinta ya ce da ita duk mutanen gidan nan basu isa duba mata y'a ba sai itace zata zauna? Ta koyi kara mana ta juyo gida ta barta koda da Akilah ne Neman rasa madafa ya sakata fitowa bayan ta saka hijab dinta ta shiga neman Mai kwanoni a cikin gidansa Da kyar ta ganshi bayan an mata iso ta duka tana sake sanar masa halin da ake ciki Sosai ya ji zuciyarsa na neman shiga wani hali, subahanallah ta sauka? Ama babu wanda ya zo ya sanar masa? Bai jima da shigowa daga wajen datawan Anguwar ba sun je neman auren jikar malam, jin shiru ya zaci ana cen ana gumurzu, bale da bai ga TAUFEEK ba ya zaci yana ciki ana taimaka mata dan ta sauka, Wayarsa ya dauka ya shiga kiran numbar TAUFEEK din Kira na farko ya daga yana yin salama Murya a hade Baba ya ce" kana ina?" TAUFEEK ya kalli HAJIA dake jan carbi tana gyangyadi, tunda KHausar ta ishe shi da kukan sai ya je ya duba Yumnah ya baro bangaren nata ya dawo wajen HAJIA wace ta masa damu da ƙanƙara tace ya sha ya KWONTA ya kuma cire damuwar kowace Shegiya babu wace zata dagawa jikanta hankali shi kuma ya yi kwoncen burinsa ya je ya dauketa ya kaita a masa hoton cikinta, ama ya san ba zata yarda ba, hasalima ya ga ta nufi wajen Mama ya tabbata tana cen sunna kwasa A tausashe ya ce" Aba ina wajen HAJIA" HAJIA ta yi firgigit ta farka daga barcin ta miko hannu tana fadin" Bani shi nan, Allah na tuba masifa muna sume ma yi muke, mai kwanoni kana ji na? Wace tsiyar kake so da jikana ne Ni? Ka fa kiyayeni an jima da shiga duniyar yancin kai tsaf nake kai karar ka a mana tsakani, yau ga neman magana , yaro sai motsewa yake saboda kun tsane shi? To Ni ina so kuma ba zan amince a lalata min kwonciyar hankalin jika na, ka fadi maganarka wa Ni in ji daidai nake da kai" Tunda ta fara fadan Baba ya sada kansa tamkar yana gabanta, a tausashe sosai ya ce" Ki yi hakuri HAJIA, ki yi hakuri dan Allah, Allah ya huci zuciyarki, babu wanda zai masa komai, dama so nake yi mu hadu da shi a cen bangaren iyalin nasa da KHausar da kuma mamansa dan a sasanta wannan rigimar domin ban ga anfaninta ba sam" HAJIA ta tabe baki ya ja tsaki ta ce" Dama du Kai ka bada kofa aka raina mana wayo, ka ringa kwasarmu kana kai mu gabanta kamar uwarmu ana ja mana kunnen mu ringa yi mata biyayya, 5 To kai dan huwa rahamanu yau karya kake yi, ka daukota ku zo nan da kai da kowama idan mun gusa daga nan Ni da Magidanci ba dije ba Sarkin mahalba ya saka min da ya haifeni, kuma ita khadijar yau in ta je CEN din da Ni kake magana dan Allah Habu ka saka khadija ta je bangaren yarinyar nan Allah kuwa sai na saka ka a tashin hankali, aikin banza aikin wofi ku wani sako ya da danta a gaba, kaniyar du shegen da ya fasa daga ita uwar Tata , da uban n......" Kitttt ya datse yana sada kai sosai domin Muryar HAJIA a bayyane yake ba a boye ba, ana jin amonta sosai fa, sai ya ji kunyar zagin da sirikan nasa suka sha , dan sarai maman Yumnah ta ji Ita din kanta ji ta yi ta fara shayin zaman nan, ama kuma da wata masifar gwara wata, da ace harda mijinta a zaman gwara a yi da iya itan a samu masalaha ta koma gidanta tun kafin babansu ya biyota A sanyaye ta mike tana fadin" Elhaji Bara mu je CEN din ai, Allah ya bada hakuri" Baba mai kwanoni ya ce" A'a HAJIA zata iya ? " Maman su Yumnah ta ce" Zata iya in sha Allah Elhaji Bara na je" A bangaren HAJIA kuwa sai da ta idasa ashariyarta tsaf harda Mama a ciki ta ce" Ba kana ji na ba?, halo mai kwanoni? Habu ina sauraranka!" Sai kuma ta dago wayar ta zubawa watsetsen screen din ido tana kankance idannu ta ce" Ka ga fuskar KHausar a saman wayar nan kamar faranti, kai Magidanci duba min idan Ya kashe bi min kiran, aikin banza yau in ban mike na kashe wamcen yaron da mari ba lalle sunnana ya koma solofiyo !" Wayarsa ya karbe yana sakar mata harara ya ce" Yanzu sunnan ubana ne kika kama, kina daf da Ni kika zagar min uba da uwa kika kare da cewa fuskar matata uwa faranti ko? Ba damuwa nace ba damuwa ama kika yarda kika taba fuskar ubana nine maganinki kin ji na fada maki!" HAJIA ta yi tsuru tana kallonsa, sai kuma ta mike tana jan tsaki ta ce" Na ce Habu, ai kai ya haifa ba Ni ba aikin banza Habu Habu habubuwa ambaliya dan dije, kai da fa tawayashi nake yi HAJIA ce tace kar ta kuma gani dan fari ina riritawa, aka shiga tsakanina da d'ana, to na ce Habu SUNNAN nawa uban ne da ba zan kama ba? In na mare shi zama aljani ka ringa firgitani in ka isa!" Fadan sai ya dawo tsakaninsu ya zabga mata harara ta rama kowane ya daure fuska! Aba kam ya jima a zaunen nan yana tunanin hanyar da zai bi ya shawo matsalar, kafin ya sauke ajiyar zuciya ya nufi bangaren su Mama ya haura ya same su Maman saman salaya KHausar kuwa tana zaune da littafi tana karatu Kai ya gyada bayan ta amsa, KHausar ta mike da sauri zata fita ya ce" Dakata, ai ba inda zaki je sai ku wuce mu je" Mama ta zuba masa ido, so take yi tace da shi shi. Yauma kaita zai yi ya tirsasata yiwa matar danta biyaya , to babu inda zata je! sai dai wanzuwar KHausar a wajen ya saka ta sada kai ta mike tana rike da carbinta ta fara yin gaba, dan ba zata taba barawa yarinyar muguwar tarbiyyar da bata ganni a gidansu ba na sa'in sa da miji! [8/17, 11:05 PM] Maman Aslam: 💔💔💔💔❤‍🩹❤‍🩹💔💔💔💔 *DA CIWO A ZUCIYATA* 💔💔💔💔❤‍🩹❤‍🩹💔💔💔💔 _MALLAKIN_ *SAJIDA NIJAR* *FREE BOOK NE* 6️⃣5️⃣ *GARABASA, GARABASA, PROMOTION, PROMOTION DIN LITATAFAN MARUBUCIYAR A KAN FARASHI MAI SAUKI 1K, YAN NIJAR KUWA 1000 FRANCS CEFA* 1: Duk karyar kada 2: Yar mahaukaciya 3: Neman na kaina 4: Bani da zabi 5: Bak'a ce 6: Kutkale 7: Makauniya ce 8: Mage 9: Duk nisan jifa 10: Idan ka raina inda kake 11: Dutse 12: Alkalamin kadarata 13: Bani da zabi 14: Dakika Biyar 15:Wata kokowar 16: Aure yakin mata 17: Ni zan ladabi 18: Daga tafia daukar soja *Dukansu a kan farashi mai sauki, zaka saka dubu guda ne domin promotion ne nake yi, ka tuntubeni kan layina kamar haka +227 93 81 16 18, Sajida Nijar* Now *Da CIWO A ZUCIYATA* *Tallah, tallah, tallah* *SECRET DE LA FEMME DU MANGA* _Gidan Kamshi, Sirrin Manyan Mata, nesa tazo kusa,Amarya ,Uwar gida,Ango da mai gida Har ma da yan mata da samari shin kuna sane da cewa HAJIYA FUSAM ta shirya tsaf domin gwangwaje ku da turarakunta masu dankaran kamshi? Tare Kayan gyaram jiki na musamman ,wanda daga nesa kamshin ki kadai ya wadatar ya isar da sakon zuwanki waje,gidan ki kuwa sai ya zam abun kwatance wajen kamshi, kar na cika ku da surutu bara in fara zayyano su_ Farar Humura Bakar Humura Humura special, humura de bain Humura epicé Lait de nuit Parfums désodorisant Parfums rideau et dras Lait de nuit Alkam Kulakcam *Waɗannan kadan ne daga bangaren turaran ruwa* Gagab, sandal flex, Durot, durus, sandal fleur, tafarce, farce, sandal bangui, sandal, hypotonic sandal, al'ut, coktail creation VIP, Gajiji, Mankaji, turaran wutar labule da cafet, Aba malan, boulettes *Munada bangaren gyaran jiki kamar haka:* mai mai saka santsin jiki, mai mai kanshi, Kayan gyaran jiki mai saka fata ta yi santsi da laushi, kayan gyaran jiki mai saka fata ta yi fari, Sabulu mai saka fata ta yi haske, sabulu mai saka fata ta yi santsi, sabulu mai goge yanayin fata, mai wanda baya saka fari mai gyara fata Sayen na gari mai da kudi gida,sai an gwada akan san na kwarai💃💃 Hajiya Fusam na zaune a kasar Niger domin yin magana da ita kai tsaye tuntuɓi wannan number 97 82 44 94 *SECRET DE LA FEMME DU MANGA* Gidan Kamshi, Sirrin Manyan Mata💃💃💃💃💃 Tallah 3 Hajiata, ke kin san rayuwar aure sai da anini, in babu jagab a babar eriya oga ya kama tofa yawu da neman yadda zai yi bawan Allah, idan kuma babar haja a bude ham ai ba labari oga sai dai ya shiga ya fito kamar ya shiga kofar ruwa😔, zo ki ji, a farashi mai rahusa zaki gwangwaje ki rike bakin Elhaji gudun tada yara, ama idan lamari ya yi lamari tsaf zaku karya gado☹️🫣 🔥💥🔥💥🔥💥🔥💥🔥💥🔥💥🔥💥 *HOHOHO WANI KAYA SAI AMALE, DON JAKI BAZAI 'DAUKA BA, INA MATA MASU BUK'ATAR 'DAGA DARAJARSU A WAJAN MAZAJENSU INA MATAN DAKE SHAN WULAK'ANCIN MIJI KO NA KISHIYA ,INA MATAN DAKESON ZAMOWA MOWA AGIDAJEN AURENSU TO ALBISHINRU MAMAN ZARAH YAR MUTAN SOKOTO TA SHIRYA TSAF DOMIN GABATAR MAKU DA ZAFAFAN KAYAN MATA MASU KYAU DA INGANCI WANDA BASUDA ALGUS ACIKI , AKWAI MAGANI DANAYI BINCIKE AKANSU DAN FARIN CIKIN MA'AURATA NAMU BA IRIN NASU BANE KAYAN MU NA DABAN NE NA ASALIN SAKKWATAWAN SHEHU MASU ABUN MAMAKI* 07034251528 kayanmu masu inganci ne masu ladaftar da kowane irin namiji Kad'an daga cikin abubuwan da muke dasu Ingantaccen maganin nono , Wanda zai gyara maki nononki donmin dawo da martaban nononki acikin kankanin lokaci komai lalacewarshi kuwa sauran bayani sai mun had'u pc +234 703 425 1528 Maganin hips (hips up) Wanda zai ciko maki da hips dinki su cika suyi bul bul ga laushi dasu k'ara suyi dass abun sha'awar kowane namiji Maganin infection Sha yanzu magani yanzu Yana fatattakar sanyi cikin kankanin lokaci magani ne na maza da Mata insha Allah kowane irin sanyi gareki kikayi amfani dasu anwuce wajan Ingantacce Kuma sahihin maganin k'iba Wanda Zaki ciko acik kankanin lokaci zakiyi kibar ki Yar dai dai misali ki huta Zama da Rama Baki rasa ci ba Baki rasa sha ba amma kullum Ana kallon cewa kinada matsala agidan aurenki saboda wannan ramar , Rama batayi ba Sam Yar uwa Sabulun wanka Kalolin sabulun tsarki Turaren tsugunno Turaren al'ajab Hatsabibin turare Da sauransu 07034251528 Kalolin gumba Gumbar Dabino Gumbar gero Gumbar madara Gumbar matsi Gumbar ukku bala'i Gumbar tada zaune tsaye Gumbar sabon budurci Gumbar sa buzu kuwa Gumbar aya da kwakwa Gumbar ridi Gumbar mazari Sarauniyar gumba 3in1 Da sauran kalolin da bansamu fadi ba, Kalolin gari Garin mallaka Garin hutar da malaminki dakan jaraba Dakan Amare Dakan Ni'ima Dakan kishiya in bakiyi bani waje Garin sa buzu kuwa Garin buje.sharkaf Garin Dan la'asar Yayan hadiya mai suna dan la'asar Original Dan goshi Original Dan goshi (sabon salo) Original man damo Original man ayu Kitsen damo Sirrin tafin kafa Sirrin farinjini na uwargida da amarya harma da yan mata Kwallin idonka idona Muna hada set na sirrin mallaka hajiya ba boka ba Mallam sai tarin sirrika kema kizama kowa agidan surenki Akwai hadin sabon budurci ga yarinyar data rasa budurcinta ta hanyar fyade ko yaudarar d'a namiji da izinin Allah akayi maki wannan hadin to an wuce wajan sauaran bayani sai mun had'u pc Kalolin tsumi Tsumin mallaka Tsumin jaraba Tsumin madarar ni'ima Tsumin tabaje Tsumin Amare Tsumin sabon budurci Tsumin nono rakumi Matan gaske Ruwan jaraba, Da sauran kalolin da ban fada ba Kalolin matsi da basuda illa ajikin mace sai dai ma sukara maki lafiyar Matsin Dan mannau Matsin mallaka Dan la'asar Sabon budurci Mak'alemata Mashahurin matsi Ukku bala'i Matsin uban budurwa Akwai gumba ta matsi wadda Shanta akeyi ga matan da basa son yin matsi Muna hada set ga wadda Allah ya jaranfa da matsalar fyade har yarasa budurcinta , muna hada mata kaya ingantattun don dawo da martabar ta, Hohohohoho in ana dara fidda uwa ake *Kyallen al'ajabi* babban sirrin mallaka mai abun al'ajabi mallaki naki don samun damar shiga cikin jerin mata masu fada aji a gidan mazajensu , KARKU manta da sunan maman zarah sokoto sayen nagari maida kudi gida 07034251528 ina maraba daku sayen daya ko sari ina Sokoto sannan ina aikawa kowane gari cikin aminci da yardar Allah Ga Wanda suke bukatar ganin kalolin kayana to suyi sarving number na suyimun magana nayi sarving number ku zaku dinga ganin kalolin kayana a status ngd sosai 07034251528 Maman zarah mabera SOKOTO Sunna karasowa suka samu tuni su Yumnar sun iso, Yumnah na zaune a kasa kafafuwanta a hade waje daya, ciwo bai barta ba na haihuwa , ama yannayin mijinta shi ya fi komai daga mata hankali, yayarta na zaune daf da ita, mahaifiyarsu na saman kujera zaunen itama, ga dare dai ya yi ama tashin hankali ya saka su idannuwansu ya kekyashe tamkar rana, ga baby ta yi shiru abinta tana barci a hannun Akilah, Hajia na zaune itama , TAUFEEK na zaunen shima ama babu mai cewa komai tun gaishe da Hajia da suka yi da TAUFEEK din wajen ya dauki shiru Kamar yadda suke zaune a kasa itama kasan ta je ta zauna daf da aunty Akilah, so take yi ta amshi babyn nan ta rungume a jikinta, tana so kwarai a bata babyn TAUFEEK dinta ta gani , ama ta san da wahala a bata shi yasa tunda ta ciro yar ta mikawa Akilah bata kuma nuna a bata ba ama tana matukar son kallon babyn ta kuma rungumeta a jikinta, ji take yi kamar itace ta kawo masa farin cikin nan, tabas ta san yana jiran wannan ranar, sai ga ranar ta zo masa wata iri, shi yasa ta so ta saka ya yi hakuri ama ya kiya, ta tabata ko menene to fa ya kai shi makura ne Baba ne ya fara magana ta hanyar yin nasiha a tausashe ya ringa bada hakuri bale Hajia da ta kasance a wajen a dole ya bi yadda take so , sosai ya bada hakuri yana fadin" Idan rai ya baci, hakuri shine abinda ya fi dacewa bawa ya yi, bai dace ace an yi irin haka ba, a zauna a sasanta shi ya fi komai, ko menene ana iya sasanta shi a yafewa junna a ci gaba da rayuwa kafin mai rabawa ta raba, dan haka ko me yake faruwa a yi hakuri shi ya fi alkhairi" Bayan ya gama nasihar da bada hakurin ne ya dubi maman su Yumnah ta bata damar yin magana Itama a tausashen da bata taba yi masu magana ba yau ta dubi Mama ta ce" Hajia, dan Allah ko me ya faru a yafi junna a yi hakuri, mu bamu yi haka dan a bata maki rai ba, kuma kin gani Yumna yarinya ce ko me zata yi sai ana mata uzuri, ki yi hakuri komai ya wuce" Mama dake zaune ta yi murmushi ta ce" Na hakura" Daga haka ta mike ta juya da nufin tafiya Baba da ya gama Sannin abinsa ne ya ce" Maman magidanci dawo ki zauna" Mama ta dakata, a dole ta juyo ta dubeshi, kafin ta dubi Hajia ta ga hararar da Hajia ke sakar mata kamar idannuwanta zasu fado , sai ta yi wani murmushin ta dawo din ta zauna daf da Hajia ta sada kanta TAUFEEK ya sauke ajiyar zuciya ya dubi mahaifiyar Yumnah da Yumnah din baki daya sannan ya kalli Aba, a tausashe ya ce" Aba, ka yi hakuri dan Allah ,ama bana tunanin bayar da hakurin nan a dunkule zai gyara Ni, dan ban me da me aka yiwa mahaifiyata ba duk wannan zaman da aka yi , wanda idan na ji ne zan iya ganewa in har zan iya yafewa ko waye, domin kaf duniya babu wanda zai wulakanta min uwa na daga masa kafa!" Hajia aka wani saki murmushi tana sake ture daurin dan kwalinta gaba ta wani ja hannun riga ya yi sama kamar zata yi dambe ta ce" Ahaf, abubuwa ai an yi su magidanci ba dan kadan ba, Ni dai abinda nake so a gane a nan a cire min wata maganar rashin kunya cewar wannan y'a yarinya ce, ke yumana dan yan gidanku baki san darajar taki uwar ba? Ni fa munafunci ne da shashanci bana so, na fada a tsaye na fada a zaune karshe nima sai na zama abokiyar gabanta, ama idan zaki tuna na fada maki ke ki kiyayi magidanci da uwarsa wa bilahilazi idan kika yarda ya gane wawa ce ke sai ya tatakaki ya kaiki gidanku a kan mamansa, ke bakima san ruwan dake wankanki ba, sarakuwa ko bata sonka neman fada kake a wajenta bale wannan da babu abinda ya dameta da lamarinku ita fatanta ku zauna lafiya? Yo Ni nan meye baba ta soro bata min ba Allah jikan rai na yafe mata iyi? Ama haka na rayu ina bin gindi kar a watsani waje , uwa ai tana gaba da komai, in ba dan iska Bama waye zai raina uwar wani? Ki dauka a kan taki uwar gatanan mana iyi? In menene kece kika fara yiwa kanki, mu muna da sha uku aka mikamu daki muka iya girmama iyayen miji bale ya'yan yanzu ya'yan salula yar latse kunna dirowa duniya kuke matse anini, kuma kun iya neman maganin mata rai a shige daka da miji, har ku ne za'a koyawa kula da uwar miji? Da abinda ke ranki dai yar nan wanda ba zai samu ba dan gaskiya ina tsoron shima ba zaki samu ba, ki sauke kanki in zaki sauke a yi rayuwa in kuma tashina tashina za'a yi in fede biri da abawa a wajen nan na irin laifukan da kika yiwa uwar magidanci kau?" Kusan a tare su uku suka nema ba sai Hajia ta fada ba, kowane da yannayin da ya yi furucinsa ama matsayar su daya ce kar Hajia ta fere biri da abawan nan da tace zata fere, da baba mai kwanoni da Yumnah da kuma mahaifiyar Yumnar Yumnah murya na rawa ta ce" Mama dan Allah ki yi hakuri, dukkan abinda na maki ki yafe min in sha Allah ba zan kuma ba, baba da Hajia dan Allah ku ba yayanmu hakuri ba zan kuma ba" Baba sai ya karra jin tausayin yarinyar ya kama shi, ko dan bai san me da me ta yin bane? Ama ko menene yana ganin ana iya yafe mata, ko menene, dan haka a tausashe ya dubi maman TAUFEEK ya ce" Hajia karama, ki yafewa yarki kin ji? Kin san yayanmu sai da hakuri, ki dauka yarki ce ta maki laifi ta kuma yi nadama kin ji?" Mama ta sauke ajiyar zuciya yanzunma a tausashe ta ce" Ni fa na jima da na yafe babansu, Allah ya shirye su ya musu albarka" Da amen aka ringa amsawa, Maman Yumnah ta sauke ajiyar zuciya ta ce" an gode Allah ya saka da alkhairi an gode sosai, kin ga ta karu Yumnar idan da hali sai a kaita asibiti dan kar ta kwana abin ya zama wahalarwa" Baba mai kwanoni kam sai ya mike gannin an samu sasantawa ya karasa ya dauki yar ya je ya duka daf da Hajia ya bude mata yar fuskar jaririyar yana murmushi ya ce" Hajia ga fa amaryar tawa, Ni sai nake gannin kamar ta fi magidancinma kyau masha ALLAH" Hajia da kwallah ta tarun mata a ido a hankali ta amshi yar tana kallo , sai ta saki murmushi ta dago tana kallon Mama da Khausar dake matsowa tana so a bata, Hajia ta sake sakin murmushi ta ce" Matso ki tayani gani Khausara, kin ga yar y'ar magidanci , kin kuwa san irin adu'ar da nake yi Allah ya nuna min, kai shedan ko dan hegiya Allah dai ya rabamu da sharinsa! Mai kwanoni ka mata huduba mana ka ji? Wani sunna za'a saka mata?" Baba na murmushi ya kalli TAUFEEK da har yanzu ba wani sakin fuska ya yi ba ya ce" Wani sunna kuka zaba ne Elhaji karami? Ka kuwa dauketa? Kamarku daya, kennan kama take da Mamanka, matso ka yi mata addu'a sannan ka duba lafiyarta idan kuwa asibitin zasu tafi sai a kai su a basu dukan kular da ta dace, Allah ya yi albarka" A tausashe TAUFEEK ya amsa da amen Aba, sannan ya sake sada kansa a tausashen ya ce" ka yi mata da sunnan Nana Khadija Aba, Allah ya raya ya yi mata albarka" Aba ya amsa da amen ya Allah, hakama dukkan wani dake wajen TAUFEEK ya dora da fadin" sai dai ina neman alfarmar a yi hakuri da maganar fitan, zan dubata da kaina, ko wanka ba zata je gida ta yi ba zata yi a nan gidan, idan akoy Wada zai zo ya zauna mata Tom, in babu Hajia zata samo duk wace ta ga ta yi ta zauna mata, sai abu na karshe, Yumnah ki ji tsoron Allah ki kuma guji fushina, ba zan lamunce ki wulakanta koda auta bane a gidan nan dan Ni ban wulakanta kowa ba a gidanku, ki sani raina mahaifiyata shine mafi munin kuskuren da zaki kuma tafkawa, domin wannan zama da aka yi yau ina mai tabbatar maki ba za'a kuma maimaitashi da Ni ba, ba zai yiwu ace kulun ina tara iyayena a kaina ba, inaga na yi girman da zan kare masu wannan tashin hankali na iyalina!, Idan har da hali zan so ki gane mu zauna lafiya, idan kin kiya Yumnah ba zan iya zuba maki ido ki wulakanta min wace ta haifa maki Ni ba, du dadin zaman da zan ji da ke lami ne idan har baki girmama min uwa ba" Yumnah da sai yanzu ta ji sanyi na ratsa zuciyarta ta girgiza kai da sauri ta ce" In sha Allah ba zan kuma ba yayanmu" a zuciyarta kuwa tana ayana' bi izinillah ba zan kuma ba, koda mama bata so na zan yi mata biyaya bale su Hajia ne ke cewa ba zata taba so na ba, sai yau na ankara da aunty tace na san basa son mijina Ni me zan masu a duniya da zasu so Ni? Kowa ta kansa yake yi, nima kuwa zan yi ta kaina, Khausar ta zama zanen kadarar rayuwata Allah ya yi sai ta auri mijina , in sha Allah zan koyi zama da ita, ina ji ina gani na haihu maimakun na zamto ina cen lulube ana jiji da Ni gani a filin Allah ko ciwon baya damuna kamar bacin ranka? Soyaya ba karya bace Ni na san ina sonka kuma zan yi maka biyaya koda kana cutar da Ni ne bale idan har na nuna ka cutar da Ni na zalunceka!' Masalaha aka samu sosai , Mahaifiyarta cike da tausayi take kallonta, lalle ta yarda da maganar da Akilah ta fada wani lokaci cewar, Mama, ki bi Yumnah da addu'a, domin son da take yiwa mijinta ya fi wanda shi yake yi mata, ki yi kokari ki ringa kwabarta kina nuna mata ta yi hakuri ta kuma iya zama da mijinta, shine kawai zai fisheta, domin ko aurenta ya mutu ita zata wahala, na riga na gane tana sonsa fiye da tunani bata iya rigima da zuciyarta a kansa, hakan ya sa take tunanin ta fi kowa sonsa, idan har zata samu ko mahaifiyarsa kar ta rabe shi, kin ga kuma son kan ya yi yawa abin zai haifar mata da damuwa, mafi a'ala shine a nuna mata TAUFEEK miji yake a gareta ba yaron gidanta ba, ba kuma abinda take kiwo ba, dole ta mutunta ahalinsa Ajiyar zuciya ta sauke ta mike ta bi bayan mai kwanoni da yace ta zo a kaita gida, Akilah kam nan zata zauna Baki daya suka dadaka suka nufi bangaren Yumnah banda Mama wace ta wuce nata bangaren dan ba zata iya binsu ba, ga Hajia ga Khausar ga Akilah ai ko menene sun isa, TAUFEEK ne ya wuce bangaren Khausar dan daukan kayan da zai mata anfani da su dan yi mata dinki Sosai ta ci azabar ɗinkin nan, du kuwa da ya kashe wajen ama waje ya riga ya fara hucewa da zafin fitowar kan d'a hakan ya sa ta sha kuka da ihu na azabar ɗinkin har ya gama mata sannan ya janyota jikinsa ya rungumeta yana share mata zufar dake tsatsafowa a goshinta A raunane ta dora kanta a kirjinsa tana shaƙar kanshin jikinsa A tausashe sosai ya furta" Allah ya maki albarka , ya raya mana Anmi, Allah ya baki ladan daukan ciki da dawainiyarsa ya sa Anmi ta zamto mai jin kan iyaye ce" Ajiyar zuciya take saukewa tana amsawa da amen , tana ji kwarai ta so cutar kanta, da kulawar da ta fi wannan ce zata samu , sai gashi ta yi sake da damarta, ama kuma ta godewa Allah da ya sa ta gane da wuri ta bada hakuri Sai da dare ya yi sosai suka tafi shi da Khausar, Hajia dama tunda aka gama ɗinkin ta tafi tana fadin zata je dan ta tashi da wuri a fitar da hatsi a yi gumbar kunnu ta mai jego da sauransu, sosai Akilah ta sake yi mata nasiha bayan an saka baby a nono tana fada mata ta yi ta adu'ar Allah ya sanyaya mata zafin kishin nan ta zauna lafiya da mijinta da danginsa da matarsa Washe gari bayan ya fito daga wajen su Yumnah ya dauki Khausar a mota ya nufi asibiti da ita Docter A'isha ce ta mata hoton cikin, ai kuwa ikon Allah sarautar Allah baby kwonce a mara gaba daya halitarsa an gama ama uwarsa bata san da shi ba bale mahaifinsa, ita da kanta docter aishar sai da ta yi godiya ga Ubangijin talikai da ya nuna mata haka, sun sani akoy irin haka ama basu gani ba, a waima suka dauka sai gashi ta gani, Khausar ta mike rasss ta mayar da hijab dinta tana kauce irin duban da TAUFEEK ke Binta da shi har docter A'isha ta gama ta fice a office din A nutse ya janyota jikinsa yana kallonta hadi da shafa mararta Kasa kasa ya ce" idan ina tune da kyau , ranar da na haye nan na bada ajiyar ko?" Khausar ta zarro ido ta juyo tana kallonsa ta ce" na shiga uku, me ya samu bakinka yake magana haka?"...... Dariar yannayinta ya yi ya ce" zuma ya sha" Ai kam yanzu sai ta yi gum dan kar a kuma fada mata wace zata saka ta wuni bata dago kanta ba dan kunya Sannu a hankali take tafiyar da yannayinta, mahaifiyarta, mahaifinta, mijinta, Hajia sai mama suka san tana dauke da junna biyu har aka yi sunna aka gama aka ci gaba da wankan jego tana nan tana rainon cikin da ya shige watansa na tara har take tunanin wai fa tana iya haihuwa itama nan da satitika gashi cikin bai kumbura ba sosai irin na masu ciki, ya dai dan tasa ama ba wani tasawar a zo a gani ba, dan har ta gaji da lamarin Hajia da shan dariyarta ko zama ta zo yi sai Hajiar tace ta zauna a hankali kar aje kan d'an a duwawunta yake dan nan dinma sake budewa ya yi da cinyoyinta, sai taunawa da suke yi a kwanakin nan Da rashin kuzari yauma ta nufi bangaren Hajia tana jin kamar ana sukanta a dukkan gaban jikinta, babu inda baya yi mata ciwo ga mararta kamar tana fama da zaki irin yadda ta daure mata take ciwo sosai Tana zama ta samu kiran TAUFEEK, yana fada mata zai shigo da wuri fa yau a dole tace bari ta mike ta sama masa wani abin domin yau girkinta ne tuni yumanh ta zubda wanka ta koma girki kusan sati biyu kennan , Mikewar da ta zo yi ta ji gaba daya jikinta ya kwashi rawa, A hankali ta shiga yin addu'a ko zata iya mikewa, ama kamar an saka wani ice an tokareta kuma an shiga nausa mata shi a gadon bayanta, wani irin ciwo mai wuyar fasara ya sakata sakon hailala tana zaro ido lokaci daya tana neman yadda zata yi ta zauna Hajia dake tankade maganin zaki na khausar din ce ta yi shiru tana saurarawa sai kuma ta mike ta fito tana fadin" Kamar ana salati, Khausara miye ke lafiya?" Hajia ta fada tana nufota da sauri gannin ta gaza tsaye ta gaza zaune numfashinta na sama sama tamkar zata sume "Hajia bayyana, marana, Hajia cikina wayo Allahna ciwo Hajia " Khausar ke fada tana rike hannun Hajia Hajia ta zaro ta ware murya ta aniya fadin" [8/18, 7:36 AM] Maman Aslam: 💔💔💔💔❤‍🩹❤‍🩹💔💔💔💔 *DA CIWO A ZUCIYATA* 💔💔💔💔❤‍🩹❤‍🩹💔💔💔💔 _MALLAKIN_ *SAJIDA NIJAR* *FREE BOOK NE* 6️⃣6️⃣ *GARABASA, GARABASA, PROMOTION, PROMOTION DIN LITATAFAN MARUBUCIYAR A KAN FARASHI MAI SAUKI 1K, YAN NIJAR KUWA 1000 FRANCS CEFA* 1: Duk karyar kada 2: Yar mahaukaciya 3: Neman na kaina 4: Bani da zabi 5: Bak'a ce 6: Kutkale 7: Makauniya ce 8: Mage 9: Duk nisan jifa 10: Idan ka raina inda kake 11: Dutse 12: Alkalamin kadarata 13: Bani da zabi 14: Dakika Biyar 15:Wata kokowar 16: Aure yakin mata 17: Ni zan ladabi 18: Daga tafia daukar soja *Dukansu a kan farashi mai sauki, zaka saka dubu guda ne domin promotion ne nake yi, ka tuntubeni kan layina kamar haka +227 93 81 16 18, Sajida Nijar* Now *Da CIWO A ZUCIYATA* *Tallah, tallah, tallah* *SECRET DE LA FEMME DU MANGA* _Gidan Kamshi, Sirrin Manyan Mata, nesa tazo kusa,Amarya ,Uwar gida,Ango da mai gida Har ma da yan mata da samari shin kuna sane da cewa HAJIYA FUSAM ta shirya tsaf domin gwangwaje ku da turarakunta masu dankaran kamshi? Tare Kayan gyaram jiki na musamman ,wanda daga nesa kamshin ki kadai ya wadatar ya isar da sakon zuwanki waje,gidan ki kuwa sai ya zam abun kwatance wajen kamshi, kar na cika ku da surutu bara in fara zayyano su_ Farar Humura Bakar Humura Humura special, humura de bain Humura epicé Lait de nuit Parfums désodorisant Parfums rideau et dras Lait de nuit Alkam Kulakcam *Waɗannan kadan ne daga bangaren turaran ruwa* Gagab, sandal flex, Durot, durus, sandal fleur, tafarce, farce, sandal bangui, sandal, hypotonic sandal, al'ut, coktail creation VIP, Gajiji, Mankaji, turaran wutar labule da cafet, Aba malan, boulettes *Munada bangaren gyaran jiki kamar haka:* mai mai saka santsin jiki, mai mai kanshi, Kayan gyaran jiki mai saka fata ta yi santsi da laushi, kayan gyaran jiki mai saka fata ta yi fari, Sabulu mai saka fata ta yi haske, sabulu mai saka fata ta yi santsi, sabulu mai goge yanayin fata, mai wanda baya saka fari mai gyara fata Sayen na gari mai da kudi gida,sai an gwada akan san na kwarai💃💃 Hajiya Fusam na zaune a kasar Niger domin yin magana da ita kai tsaye tuntuɓi wannan number 97 82 44 94 *SECRET DE LA FEMME DU MANGA* Gidan Kamshi, Sirrin Manyan Mata💃💃💃💃💃 Tallah 3 Hajiata, ke kin san rayuwar aure sai da anini, in babu jagab a babar eriya oga ya kama tofa yawu da neman yadda zai yi bawan Allah, idan kuma babar haja a bude ham ai ba labari oga sai dai ya shiga ya fito kamar ya shiga kofar ruwa😔, zo ki ji, a farashi mai rahusa zaki gwangwaje ki rike bakin Elhaji gudun tada yara, ama idan lamari ya yi lamari tsaf zaku karya gado☹️🫣 🔥💥🔥💥🔥💥🔥💥🔥💥🔥💥🔥💥 *HOHOHO WANI KAYA SAI AMALE, DON JAKI BAZAI 'DAUKA BA, INA MATA MASU BUK'ATAR 'DAGA DARAJARSU A WAJAN MAZAJENSU INA MATAN DAKE SHAN WULAK'ANCIN MIJI KO NA KISHIYA ,INA MATAN DAKESON ZAMOWA MOWA AGIDAJEN AURENSU TO ALBISHINRU MAMAN ZARAH YAR MUTAN SOKOTO TA SHIRYA TSAF DOMIN GABATAR MAKU DA ZAFAFAN KAYAN MATA MASU KYAU DA INGANCI WANDA BASUDA ALGUS ACIKI , AKWAI MAGANI DANAYI BINCIKE AKANSU DAN FARIN CIKIN MA'AURATA NAMU BA IRIN NASU BANE KAYAN MU NA DABAN NE NA ASALIN SAKKWATAWAN SHEHU MASU ABUN MAMAKI* 07034251528 kayanmu masu inganci ne masu ladaftar da kowane irin namiji Kad'an daga cikin abubuwan da muke dasu Ingantaccen maganin nono , Wanda zai gyara maki nononki donmin dawo da martaban nononki acikin kankanin lokaci komai lalacewarshi kuwa sauran bayani sai mun had'u pc +234 703 425 1528 Maganin hips (hips up) Wanda zai ciko maki da hips dinki su cika suyi bul bul ga laushi dasu k'ara suyi dass abun sha'awar kowane namiji Maganin infection Sha yanzu magani yanzu Yana fatattakar sanyi cikin kankanin lokaci magani ne na maza da Mata insha Allah kowane irin sanyi gareki kikayi amfani dasu anwuce wajan Ingantacce Kuma sahihin maganin k'iba Wanda Zaki ciko acik kankanin lokaci zakiyi kibar ki Yar dai dai misali ki huta Zama da Rama Baki rasa ci ba Baki rasa sha ba amma kullum Ana kallon cewa kinada matsala agidan aurenki saboda wannan ramar , Rama batayi ba Sam Yar uwa Sabulun wanka Kalolin sabulun tsarki Turaren tsugunno Turaren al'ajab Hatsabibin turare Da sauransu 07034251528 Kalolin gumba Gumbar Dabino Gumbar gero Gumbar madara Gumbar matsi Gumbar ukku bala'i Gumbar tada zaune tsaye Gumbar sabon budurci Gumbar sa buzu kuwa Gumbar aya da kwakwa Gumbar ridi Gumbar mazari Sarauniyar gumba 3in1 Da sauran kalolin da bansamu fadi ba, Kalolin gari Garin mallaka Garin hutar da malaminki dakan jaraba Dakan Amare Dakan Ni'ima Dakan kishiya in bakiyi bani waje Garin sa buzu kuwa Garin buje.sharkaf Garin Dan la'asar Yayan hadiya mai suna dan la'asar Original Dan goshi Original Dan goshi (sabon salo) Original man damo Original man ayu Kitsen damo Sirrin tafin kafa Sirrin farinjini na uwargida da amarya harma da yan mata Kwallin idonka idona Muna hada set na sirrin mallaka hajiya ba boka ba Mallam sai tarin sirrika kema kizama kowa agidan surenki Akwai hadin sabon budurci ga yarinyar data rasa budurcinta ta hanyar fyade ko yaudarar d'a namiji da izinin Allah akayi maki wannan hadin to an wuce wajan sauaran bayani sai mun had'u pc Kalolin tsumi Tsumin mallaka Tsumin jaraba Tsumin madarar ni'ima Tsumin tabaje Tsumin Amare Tsumin sabon budurci Tsumin nono rakumi Matan gaske Ruwan jaraba, Da sauran kalolin da ban fada ba Kalolin matsi da basuda illa ajikin mace sai dai ma sukara maki lafiyar Matsin Dan mannau Matsin mallaka Dan la'asar Sabon budurci Mak'alemata Mashahurin matsi Ukku bala'i Matsin uban budurwa Akwai gumba ta matsi wadda Shanta akeyi ga matan da basa son yin matsi Muna hada set ga wadda Allah ya jaranfa da matsalar fyade har yarasa budurcinta , muna hada mata kaya ingantattun don dawo da martabar ta, Hohohohoho in ana dara fidda uwa ake *Kyallen al'ajabi* babban sirrin mallaka mai abun al'ajabi mallaki naki don samun damar shiga cikin jerin mata masu fada aji a gidan mazajensu , KARKU manta da sunan maman zarah sokoto sayen nagari maida kudi gida 07034251528 ina maraba daku sayen daya ko sari ina Sokoto sannan ina aikawa kowane gari cikin aminci da yardar Allah Ga Wanda suke bukatar ganin kalolin kayana to suyi sarving number na suyimun magana nayi sarving number ku zaku dinga ganin kalolin kayana a status ngd sosai 07034251528 Maman zarah mabera SOKOTO Ke Hamdiya, kirawo min mamanku , Khausara haihuwar ce? La ha ila ha ilalahu Muhammadu rasululahi sallalahu alaihi Wasallam yau ga abu, yar nan dan mutun din zai fito yanzu? Wayo Ni rikeni da kyau rikeni" gaba daya sambatu Hajia ke yi tana fadin a riketa bayan hannunta kawai da Khausar ta riko sai tangal tangal take yi Ba'a wani jima ba da tafiyar Hamdiya sai ga su Maman har sunna rige rige domin da ta shiga da gudu ta samu su Hajia a falo sunna fira suka tambayeta dalilin gudunta ta sanar masu Hajia ce tace a kirawo mama wai Khausar zata haihu, shine abin ya wani irin dakarsu Mamanta ta shiga yi mata fadan wani irin haihuwa sai kace abin wasa wace Khausar din ce zata haihu, ina cikin a jikinta? Bata son iya shege da karyar banza, ita kuma ta sanar mata ita dai haka Hajia tace, shine suka mike suka fara fitowa dan gannin me ake nufi kuma? Dama yanzun tsakaninsu da Yumnah idan ta shigo ta gansu ta gaishe su ta yi gaba, dama yarinyar sun san ba kunya ce da ita ba gwarama Khausar din a kanta dan kiri kiri yanzun take masu kallon raini da gani gani, gaisuwarma ta yiwu ta rainin ce ba ta mutuntasu ba Karasowar Mama da akwatin Khausar din ne ya saka Hamdiya karba ita din kanta cike da mamakin haihuwa kuma? Gaba daya sunna bin Khausar din da kallo da Hajia dake mata sannu domin ya lafa mata tun dazu Mama ta yi murmushi ta ce" Hajia ko sai juyi ne aka yiwa yar gidan naki? Na ga ta lafa ko?" "Wai wani irin ciki, a ina cikin?" Hajia nawarah ta tambaya dan ta gaza yin shiru da bakinta, du kuwa yadda TAUFEEK ya gindaya masu sharuda tsakaninsu da matansa da mahaifiyarsa ba zasu iya ganni su kyale ba, Mama ta mata banza bata bata amsa ba, ta dai zuba masu ido tana kallon yadda Hajia ke tausar Khausar din domin har yanzu kaffafuwanta rawa suke yi Hajia ta dago tana duban su Hajia nawarah ta ce" Wai waye ya yi kiranku? Ni fa bana son rainin hankali ku fa kiyayeni yau ba zan dauki tsuguni tashinku ba, ku tashi ku bani waje ko na gwada maku naku rashin da'ar fatiha ce a kan nawa!" Kunya ce ta rufe su, ba'a taba haka ba, du abinda zasu yi Hajia bata taɓa dizgasu irin na yau ba, ba shiri suka mike suka wuce , kowace na ciki na ciki suka ga shigowar motar TAUFEEK da matsiyacin gudu Mama ta dubi Hamdiya dake zaune tana jijiga Anmi ta ce" Hamdiya tashi ki kai takwarar Hajia wajen Mamanta ki ce da ita zamu kai yar uwarta asibiti ne kin ji?" Hamdiya ta amsa ta kama hanyar fita wani ciwon ya sake tasowa Khausar mai zafin gaske , dan har numfashinta ke neman barin gangar jikinta irin Yadda take fuzga ya dagawa harta mama hankali , tana shirin sake buga masa waya ya shigo jikinsa da kayan aikinsa kuma ba shi daya bane harda docter biyu mata suka karaso ya duka yana rike da hannunta irin yadda take gumi a dole suka kamata suka nufi asibiti dan ko ba nakudar bace lalle akoy matsalar da ta haddasa wannan rikicewar tashi dayan ga numfashi na barazana Ashe wasa farin girki ne, budewar taron ne ya zo da haka, a hankali ta fara fita a hayacinta, ya zamto su kansu wa'inda suka rakata hankalinsu ya fara fita daga jikinsu Bama kamar TAUFEEK wanda a yau sai da wa'inda ke karkashin sa suka tausaya masa dan kai kawo kawai yake yi daga cen office dinsa zuwa dakin da aka kwontar da ita ana aunata ana kuma bin nakudar Tata mai tafiyar wahainiya domin tun safe har dare cenjin ƙalilan ne , har ya fara maganar idan aiki za'a yi mata gwara a yi mata ta huta dan zuwa yanzu ko idannuwanta bata iya dagawa, hawayen kuwa sun dauke cak tunda tanda fara wahala mai sunna wahala, dan ko da mahaifiyarta ke mata addu'a jinta kawai take yi, Mamanta kanta tana wani hali dan ta san irin wahalar da take sha ne yar Tata zata sha wajen haihuwa, daukan ciki da rainonsa basa shan wahala sai haifo shi, ita din kanta an sha sadakarwa ba zata yi ba sai kuma Allah ya budi ido, dan haka ta dukufa da addu'a, mahaifinta kuwa ya kasa zama ya fito ya tafi ake zaman jiran da shi Wahala kam Khausar ta sha ta, har an fara shirin kaita dakin fashi nakudar ta tashi gadan gadan , nan likitocin nan biyu suka sake dukufa kanta Allah ya bada iko aka ciro baby boy mai girman gaske domin su da kansu sun yi mamakin girman yaron masha ALLAH aka saka shi dakin kula da yara sannan aka shiga kula da ita dan ta samu kari aka dinketa aka gyarata sannan aka maidata kujerar turawa aka turata dakin hutunta wanda ke hade da dakin haihuwar cen ciki aka kuma kai mata babynta aka ajiye gadonsa daf da nata sannan aka ba family dinta damar shiga Aba na tsaye yana shi mata albarka Hajia na sake hailala da kuma buda yaro sai ta kalli jama'ar dakin ta ce" wa bilahilazi ka ga haihuwa , ɗan nan ai zai yi kilo shida masha ALLAH" Sai da TAUFEEK ya gaji da kara ya karbe babynsa ya rungume idannuwansa kuwa sun kasa bashi hadin kai dan dauke dubansa daga kan Khausar ko dan sirikai dake wajen, karshe dai dole suka wuce aka bar su da Hajia da shi da baby, Khausar na barcin gajiya har safia ya waye aka sallame su, Sosai haihuwar Khausar ta ba mutane mamaki ciki harda Yumnah, dan du irin kamewarta a gaban Khausar sai gata zaune tana sake mamakin abin tana tambayar wai dan Allah da gaske haihuwa dai haihuwa? Su Aisha da Rukaya na yi mata daria domin yadda take nunawar irin abin kamar dai wasa? Wai a ina cikin? Har aka yi ma Khausar wanka sosai ta fito tana yi mata murmushi ta ce" Aunty Khausar wannan haihuwa mai sauki haka? Allah ya sa a gama ta lafiya" Khausar ta zauna da zumbulelen hijab dinta tana murmushin itama ta ce" Aunty Yumnah ke dai a yi sha'ani kawai, ama an ji jiki ba laifi sai dai alhamdulilah ga d'anki nan mai rigima" Yumnah ta yi yar dariya ta sake leka babyn dake shan barci ta ce" Ai ya sha rigimarsa khalifana, hafizi ne bi izinillah" Haka dai haka ne firarsu, har kowa ya watse a bar mai jego da mai yi mata zama sai angon karni dake ta kai kawo dan bini bini zai shigo da kansa ne wai dan ya ji yaya jikinta ya kuma dauki Khalifa ya yi ta riritawa, ga Hajia gefe , barci ke maidata bangarenta, tana rike da Elhaji auta kamar yadda ta masa lakabi, dan tana cewa bai tashi zuwa ba sai da lokacin hajji ya zagayo Elhaji auta sunnansa An ci sunna lafiya, Khausar da TAUFEEK sun tashi da sha tara ta arziki na yan uwa da abokan arziki, Khausar ta samu alkhairi harda na mamaki sanadiyar haihuwar nan , uwa uba ga soyayar mijinta da ta danginsa abin sai godiyar Allah Bayan sati biyu ta nuna zata je wanka dan take takensa ya fara bata tsoro irin yadda ya fara yi mata wa'azin kwana arba'in al'ada ce ba adini ba sai ya nuna mata a'a ba wannan maganar bai bar yar uwarta ba idan ya barta bai yi adalci ba, a dole ta hakura sai dai ta tarki guduwa bangaren Hajia ko mama ta yi zamanta a duk lokacin da ta san yana iya ritsata, dan dinkinta ba wani gama warkewa ba ya yi, ita tana ji a jikinta idan injin TAUFEEK ya dawo wajen nan yanzu tana iya suma dan azaba shi yasa take tatala lafiyarta kar ya balata Kwonci tashi saura kwana hudu su yi arba'in, yau ta je bangaren Hajia an yi mata kunshi ya bushe har ta wanke, Hajiar kuwa na goye da Khalifa tana jijiga dan ya yi barci , Khausar din kuwa tana tsaye tana gugar tv din falon Hajia Taufeek ya shigo da salama ciki ciki yana sauke dubansa a kan Hajia ya sakar mata harara itama ta rama tana tura baki gaba ta ce" Aikin banza , ko uban me aka zo min falo da ranar gari namiji sai bin mace duk inda ta yi, an dai ji kunya su magidanci" TAUFEEK ya ja ya tsaya ya ce" Hajia ki fita a idona na rufe, an zo din ki yi gutsi gutsi da Ni,, Malama sai neman magana bi da matata har an isa a hannani zuwa inda take! Ke Khausar wuce mu je" Khausar ta yi tsuru tana kallonsa, Hajia ta sakar mata harara ta ce" Sai ki bi shi ya kuma dura maki abin asahi ki zo kina juwa uwa wace ta sha maye , ki kiyayi magidanci da kike ganninsa a nan ya aifa ki du shekara ba zai dame shi ba sai dai cen ku ku rabaje ba ruwansa abinsa ya kyalo wata ya karra!" "Hajia ki ji tsoron Allah, Ni din?" TAUFEEK ya fada yana zarro ido ya nufi wajen da Khausar ke tsaye ya ce" zo mu je ki ga kayan nan da aka kawo ki bar Hajia banda aikin mutanen yanzu saka ido babu abinda ta iya salon ta sa ki kwana Mala'iku na aikin da Allah ya umarce su saboda aikin ba daidai ba da kike yi, wuce mu je" Khausar ta dauki hijabinta tana murmushi ta bi bayan mijinta hankali kwonce tana ji Hajia na fadin binsa zaki yi Khausara? Ta yi gaba dan idan ta zauna din Hajiar ce zata wanketa tass tace bata kokari ta kwaci soyayar miji gana nuku nuku, babu ranar banza sai ta mata dure duren kayan gyara, wani lokacin mararta ta daure taf ba mai dan taimakawa, kai gwara ta je ta samu ladan nan itama na wannan rana Alhamdulilah Alhamdulilah Alhamdulilah Sai mun hade a sabon labarina bi'izinilah mai taken *AZAL*