Wani irin kallo yake bin Na'ima da shi yayin da yakejin kwakwalwar sa nawani irin juyawa zuciyar sa kuwa bugu yake kamar zai faso kirjin sa yafito, System ɗin gaban sa yature gefe kana cikin jan numfashi haɗe da huci yace "Me kike son faɗa ne kam me kike nufi?!". baki ta karkata tace "Ina nufin akan gado na samesu sarkafe da juna suna ai kata baɗala". ɗan sakai ta maganar nata tayi kana tashiga jan hanci tana matse ido da karfi wasu gun tayen hawayen da suka fito takai yatsa ta sharce kana cikin murya mai kamada mai sonyi kuka tacigaba da faɗin. "Wlh abun nan ya jima yana dami na, Ni nasan akuyata tayi kuka nasan bani da hakuri amma bazan iya cin amanar aure ba,bazan iya cigaba da zuba ido ana ha'intar kaba bazan iya gani ka karɓi ɗan shege a rashin sani ba,kayi tunani da kyau taya za'ayi cikin wata guda ya zamo naka bayan a cikin watan baka garin kuma ka barta bata da sarki". da karfi ya furta "Ya isa!". ya mike tsaye cikin jin yanda kansa ke juya masa yanufi cikin bedroom ɗin sa. bayan sa tabi da kallo har yashige yarufo kofar da karfi, sai ta saki wani murmushi tamike ta koma side ɗin ta tanajin zuciyar ta wasai... Wani irin bugawa kirjina yayi da mugun karfi acikin baccin da nake wan da nakoma bayan sallar asuba, afirgice na mike zaune tare da dafe kirjin da yake harbawa da karfi-karfi. jikina na rawa na zamo daga kan gadon na nufi kofa da sauri na fita ta cikin babban parlour nabi nanufi side ɗin sa da sauri na tura kofar bedroom ɗin sa yayin da na dafe kirjina da hannuna guda, ya na tsaye cikin ɗakin yabai wa kofa baya da sauri na isa na rungumo shi ta baya,tare da manna kirjina da ki bugawa da karfi cikin bayan shi. "Ya SALEEM". nakira sunan shi muryata na rawa, juyowa yayi yaciro ni a jikinsa da karfi tare da watsa min wani irin kallo, fuskarsa ta rikiɗe takoma irin fuskar Ya SALEEM ɗin baya babu wasa ko annuri kan fuskar nasa, cike da fargaba da tsoron ganin yanayin sana cikin muryar kukan da ya suɓuce min nace "Ya SALEEM wani mutuwar a ka kuma ko? dan Allah ka faɗa min yanzu ba sai naje gida ba kafaɗa min kawai nima na mutu ko zan huta da azabar da nake ji cikin zuciya ta". hannuna ya damko da karfi ya janyoni ya nufi kofa dani cikin muryar kuka nacigaba da faɗin "Ya SALEEM karka kai Ni ka nuna min gawar wani, mutuwa zanyi". baiyi magana ba bai kuma sake hannuna ba har muka fito cikin parlour'n sa,kana ya saki hannuna cikin fusa tacciyar murya wanda ko a da can baya kafin zuwa na gidan da kuma farin zuwana gidan ban taɓa jin yayi min magana da irin saba yace "Waye uban sa!!?". bin in da ya sauke yatsar sa nayi da ido kana naɗa go na kalli fuskarsa da babu ko ɗigon annuri cikin rashin fahimta nake kallon sa. wani uban tsawa ya buga min tare da kuma faɗin "Waye uban sa nace!". wani irin zabura nayi da jin sawan da ya bugamin ya kuma danna yatsarsa da ke kan cikina sosai,nan take abun da ke cikina ya motsa da karfi. jikina na rawa na kai yatsata sai tin kirjin sa nace "Gashi nan". hannuna ya bige da karfi cikin kuma tamke fuska yace "Raina min hankali zakiyi faɗa min waye shi waye shi da har zai haɗa muhalli da ni!". kuka na sake da karfi ina faɗin "Kai ne uban sa Ni bansan wani ba Ya SALEEM dan Allah ka dai na min wannan wasan kai ne uban sa kaine-kaine!". nafaɗa da karfi. ida nunsa ya ɗaura cikin nawa kana yace "Ni abokin wasan kine da zan miki wasa in tan bayeki uban sa kice ina miki wasa akan bakisan uban nasa bane ko..." da karfi na rufe idanuna batare da na bari ya karasa faɗar abun da zai faɗan ba nace "Ni ban sani ba, ban sani ba, ban sani ba, ban san kowa ba Ni kai nasa Ni kai ne uban sa". nafaɗa da karfi cikin muryar shashsheka da toshewar kwakwalwa da gaza fahim tar in da ya dosa. "Uban sa shi ne wan da yake sajewa da kayan makarantar su yazo yagama abun da zaiyi yafita, ai rana dubu ta ɓarawo rana ɗaya ce tak na mai kaya". cak na ji kukan da nake ya tsaya a hankali na juyo in da naji maganar ke fito wa, Na'ima nagani tana tahowa cikin parlour'n cikin isa da izza ta karaso cikin parlour'n tana cigaba da faɗin "Ai ita da ma haka rayuwa take zaka daɗe kana tsula tsiyar ka rana ɗaya tak a sirin ka ya tonu, baki taɓa tunanin zuwan wannan ranar bako?". da ɗinbin mamaki nake kallon ta yayin da naji abun dake cikin kwakwalwa ta yana son fin karfin tunanina,kai na na dafe da karfi jin yana min wani irin mugun sara. maganar ta nakuma sinkayo wa "Da auren ka karika kawo maza cikin gidan auren ka wannan wace irin rayuwa ce". zuwa yanzu kam na fahimci duk inda batun nasu ya dosa da sauri na waigo in da take nashiga girgiza kai tare da faɗin "Aunty Na'ima kiji tsoron Allah me kike son faɗa a kai na". kugu ta rike tace "Amma gaskiya yarin yar nan to in banji tsoron Allah ba tsoron ki zanji abun da kike ai katawa ne yau ashirin ki ya toni bazan taɓa zuba ido a haifo ɗan shege cikin gidan nan a matsayin ɗan gidan nan ba, da ma nasan zaki musa dan bakiyi zaton ranar tonon asiri irin na yauba". kallon ta ta maida kan Ya SALEEM da ya zube kan kujera tare da dafe kansa da hannayen sa biyu tace "My SALEEM Ina da shaidu kwarara guda uku wan da duk wani abun da ke faruwa a cikin gidan nan suna gani sun ma rigani gani, kuma ko Kotun koli ne zanje da su". tsayuwar ta ta gyara ta dubi kofa kana ta buɗe murya tace "Baba Mai gani,Sani direver Habu mai shara". Da sauri na juyo jin an turo kofar da sallama, baba mai gani na gaba Habu da Sani suna biye da shi,suka karaso cikin parlour'n kan su a kasa, a kasa suka zauna taɗan gefe kana baba mai gadi yakuma sunkuyar da kai yace "Gamu Hajiya". baya tayi ta zauna kan kujerar da ke bayan ta kana ta dube su sannan ta mai da duban ta kan Ya SALEEM, da har lokacin hannunsa na dafe a kansa idanunsa sun kaɗa sunyi jajirr sannan tace "Waɗan nan sune shai du na kuma duk kanin su sun rigani sanin abun da ke faruwa amma gasu kaji daga bakin su ranar wanka ba'a ɓoye cibi".. Bin su yayi da ido har lokacin bai furta komai ba dan yan da yake jin kansa ya zarce tunanin mai tunani. cikin wani irin bakar yanayi yakuma duban su kana yace "Wa yake zuwa gidan nan bayan bana nan?". ganin ya zuba musu ido yasa baba mai gadi gyara zama ya daɗa yin kasa da kai kana yasoma magana "Allah ya huci zuciyar ka ranka shidaɗe,wata ranar da kayi tafiya da yamma ina zaune a bakin get naji ana ƙwanƙwasa kofa sai na mike naje na buɗe karamar kofa naleka, sai naga wani ɗan matashi tsaye da kayan makaranta a jikinsa nan nake tan bayar sa lafiya gurin wa yazo yake buga kofa,shine yace min shi ɗan makarantar su HAMDAH ne gurin ta yazo dajin hakan kuma da ganin sa da kayan makarantar nasu sai na buɗe masa kofar yashiga, to ina dai daga zaune lokacin tun da yashiga kuma bai fito ba sai daf magriba, washegari yakuma dawowa da littattafai a hannunsa yace min wai zaije koya mata karatu ne ita takira sa,to tun daga ranar ya jera sati yana zuwa da kayan makaranta sai daga baya kuma ya dawo zuwa da kayan gida". yana kai wa nan yakuma yin kasa da kai cikin nuna tsantsar gaskiya. Sani ya nisa kana yace "Oga ranar ina cikin wanke mota nima na gansa ya shige cikin side ɗin ta da kayan makaranta a jikin sa, to nima dai kusan kullum sai na gansa yashigo kuma lokacin da kayi tafiyar nan ne, wata rana kuma ina daga cikin parking space na hango su sun fito tana yi masa rakiya sai dai daga bakin kofar side ɗin ta ta tsaya shikuma yafita". Zama Habu ya daɗa gyarawa kana ya fuskanci Ya SALEEM da kyau kana yaso ma magana yayin da yayi kasa da kansa yace "Oga lokacin da kayi tafiya kana da kwana 25 ranar ina cikin sharar yamma da sauri dan ranar na makara har gurin ya fara rufawa ina cikin share ta bayan ɗakin ta ta gurin window najiyo dariya sosai na tashi kuma muryar na miji ne, to ban kula ba dai nacigaba da sharana dan a tunani na kunne nane yaji min karya dan nasan dai baka gari, to can kuma sai narikajin muryar na mijin dai to da nagama sharana har zan wuce sai narika jin wasu ƴan maganganu haka, sai kuma na leka sai naga wani mutum a kan gadon ta abun dai babu kyan gani, to a lokacin naji muryar Hajiya tana rafka salati shine na zago da sauri". Sani ya karɓi maganar da faɗin "Nima ganin Habu da sauri ya shiga cikin side ɗin ta da kuma ihun Hajiya da nake jiyowa shine muka rufa masa baya nida baba mai gadi to shine muka tadda mutumin yana fito wa daga ɗakin ta"... Kamar a mafarki haka nake jin maganar nasu sai na rika bin bakin kowannen su da kallo duk wan da yakarɓi maganar sai na zubawa bakin sa ido har sai yakai karshen maganar nasa, gaba ɗaya ƙwaƙwalwa ta tatsaya cak ta dai na ai ki, bazan iya fasalta yanayin da nake ciki ba sai dai inaji a lokacin in da mutuwa zata ɗauke ni da taga ma yimin gata a rayu. tabbas na yarda da cewa in kaga kana kuka to shima wata rahama ce da sassauci wa zuciya, idanuna sun kafe sun bushe babu ko ɗigon hawaye a cikin su, numfashi na sai yi yake kamar zai bar jikina da zai tafi da yayi min babbar gata a lokacin. Maganar Ya SALEEM najiyo a sama "Meyasa duk waɗan nan abubuwan suna faruwa ba wanda ya taɓa faɗa min? har da kai mai gadi in su tunanin su bai kai nan ba ai kai duk kanin mu ka haife mu kana kallon ɓarna na wanzuwa bazaka sanar a magance abun da wuri ba". kasa baba Mai gadi yadaɗa yi da kai kana yace "Allah ya huci zuciyar ka gudun faruwan wata matsalar ce yasa ban sanar ba". da hannu yayi musu alama da kofa kana yace "Ku tashi kuje". da sauri suka mike sukayi waje Na'ima ma ta mike tanufi side ɗin ta. sai a lokacin na sami damar janyo numfashi na. idanunsa ya rumtse da karfi kana ya mike zumbur ya damko hannuna cikin tsananin bakar ɓacin rai da kunar zuciya. kai nashi girgizawa jin yan da harshe na yayi min wani irin mugun nauyi nakasa koda iya matsa shi bare na iya furta wani abu da kyar nakuma iya jan numfashi tare da faɗin "Wlh Ya SALEEM ban san komai ba ban san komai game da wannan maganar ba wlh na rantse da Allah duk abun da suka faɗa ba gaskiya bane Ya SALEEM cikin nan naka ne kai ma kasan naka ne". hannuna yakuma damkewa da karfi kana ya yarfamin wani marin da saida naji jina ya tsaya na ɗan wani lokaci,cikin kakkausar murya yace "Kada ki sake dan ganta ni da wannan kazamtaccen cikin Ni ba uban sa bane kada ki yaudari kanki da abun da ke cikin cikin ki kan cewa Ni uban sane". sai kuma ya sassauta murya ya ɗaura idanunsa kan fuskata kana yace "Akan me yasa zaki hori zuciyata da wannan mummunar horon me na gaza miki da har bayan bana nan zaki kawo wani cikin gidana harkan shin fiɗin mu har ki isar dashi muhallin da ni kaɗai na dace dashi?? Jeki na haramta kaina gare ki,jeki nace!!". yafaɗa cikin karaji tare da hangizani, nayi tangal-tangal kamar zan faɗi kasa, wani irin motsawa cikina yayi har sai da nakai hannu na dafe cikin,a fusace ya maso ni tare da kuma ruko hannuna yafisgo ni yanufi kofa yabuɗe ya hangizani waje cikin nuna Ni da yatsa yace "Tafi na daina ganin ki na dai na ganin wannan kazamtaccen cikin na haramta kai na gare ki!". yakuma nanata karmar haramta kansa a gare ni a karo na biyu, yana kaiwa nan yaja kofar ya rufe da karfi. "Innalillahi wa'inna'ilaihirraji'un". nafurta da karfe sai kawai naji wani kuka yazo min da sauri mai haɗe da gudu na juya tare da fashewa da kuka mai tsanani nanufi side ɗina, koda nashiga bedroom rasa me zanyi sai narika zaga cikin ɗakin ina cigaba da kuka nakai tsawon minti 10 ina zaga cikin ɗakin da kuka narasa meke min daɗi me zanyi guda ɗaya, sai a lokacin na juya na isa gaban wardrobe na tuɓe kayan jikina na ciro riga da zani na atamfa nasa na zura hijabi na janyo akwatin da lokacin rasuwar Inna yakai min kaya a ciki tun da na dawo na aje akwatin ban kuma bi ta kansa ba kayane kala biyar a cikin na janyo nayi waje. Ina fita naga Salele tsaye a can gefe yayi jigum ya zubawa kofar side ɗin ido,muna haɗa ido da shi sai ya girgiza min kai tare da share wasu kwallar da suka zubo mishi,juyawa nayi nasoma tafiya in da tafiyar kawai nake amma bana sanin in da nake jefa kafata, har nafita daga gidan na tari mai a dai-daita ko da muka isa na sau ka nace masa bari naje na amso masa kuɗi ganin yan da nake kuka yasa mai napep ɗin cewa nabar shi Allah ya jikan rai. dan shi a zaton shi mutuwa akayi. A farfajiyar gida na yar da akwatin ina jin mai gadi yana tanbaya ta lafiya ban ko juyo ba nayi ciki da sauri, A parlour na tadda Ummi zaune ganin yan da nashiga yasata mikewa da sauri tana faɗin "Ke HAMDAH menene?". rungume ta nayi tare da kuma kara sautin kuka na, a kiɗime Ummi taci gaba da faɗin "Menene me yafaru??". ban iya cewa komai ba sai rusar kukan da nake. Jijjiga ni tayi tace "Ke HAMDAH ki nutsu ki faɗa min menene menene kuma???". cikin muryar kuka sosai nashiga faɗin "Ummi wlh cikin sane narantse da Allah cikin sani". cikin rashin fahimta da soma shiga damuwa da ganin yan da nake maganar kamar numfashi na zai kwace tace "Cikin wa? menene ya sami cikin?? kinutsu ki faɗa min". hannunta na rike da karfi cikin fizgar numfashi nace "Ya SALEEM Ummi Ya SALEEM Ni ban san komai ba ban san me suke faɗa ba na rantse Ummi ban san komai ba".. da sauri goggo Hauwa da Aunty Halima suka fito suna faɗin "Menene me ya same ta?". Ummi tace "To ni ma dai ban sani ba ganin ta kawai nayi kamar an jefo ta". goggo Hauwa ta ruko ni tace "Ke HAMDAH wani abun ne yafaru a gidan naku?". kai nashiga gyaɗa mata tace "To menene". Nace "Goggo Ya SALEEM ne Ya SALEEM ne". sai kuka yaci karfina,gaba ɗayan su jikinsu yagama mutuwa cikin hanzari Ummi ta nufi ɗakin Abba kasan cewar yau Saturday ne yana gida,a tare suka fito da shi har lokacin ina rike a hannun goggo Hauwa,tsawa Abba yabuga min yace "Ke wai meye haka kin bi kin tadawa mutane hankali da safen nan". kokarin danne kukan nashiga yi dan nasan halin Abba shi ba irin Abbu bane mai jurar rarrashi,karaso wa cikin parlour'n yayi yana kuma faɗin "In bazaki faɗi abun da ya same ki ba yi waje kije kiyi kukan naki,ina SALEEM ɗin yake?". toshe bakina nayi da tafin hannuna cikin jan shashsheka nace. "Yace na tafi ya haramta kaishi gare ni wai cikin ba nashi bane". na karasa cikin kuka sosai. wani irin zabura su goggo Hauwa sukayi Ummi kam sai da tayi baya ta zauna kan kujera tare da ambaton sunan Allah, goggo Hauwa da Aunty Halima suka shiga rafka salati goggo Hauwa ta buga kirji tace "Ya haramta kansa da ke ya sake ki fa kenan kuma ciki ba nashi ba SALEEM ɗin shaye-shaye yakoma"... Abba ma sai da ya girgiza da jin abun da nafaɗa da sauri ya juya yakoma ɗaki. Number Ya SALEEM yakira yace yazo yanzu-yanzu yana niman sa. a parlour kuwa zaunar dani goggo Hauwa tayi suma suka zazzauna kowa jikin sa yagama sanyi,a hankali naci gaba da kuka na. batare da ɓata lokaci ba motar sa yashigo gidan duk muna zaune a parlour har da Abba yayi sallama yashigo, gefe da Abba yasamu guri yazauna a kasa kana yashiga gai da Abba da su Ummi, Abba ya nisa tare da gyaran murya yace "SALEEM wai me ke faruwa ne tashigo ta ɗagawa mutane hankali da koke-koke da wasu magan ganun da babu daɗin ji wai kace ka haramta kanka gare ta da kuma ciki wai ba naka bane ko mene?". sautin kuka na kuma karawa jin yadda zuciya ta ke tafasa, sawa Abba ya buga min yace "Zaki rufawa mutane bakine ko sai nazo gun kiyi Mai dalili!". kai na na jingina da kafar goggo Hauwa ina kukan a hankali. muskutawa yayi kana yaɗan yi kasa da kansa yace. "Eh Abba gaskiya ne abun da tafaɗa". basu Ummi kaɗai ba hatta Abba sai da ya girgiza, goggo Hauwa ta waro ido tare da buga kirji tace "Kai SALEEM kan ka ɗaya kuwa kasan abun da kake faɗa kuwa?". Abba ya gyara zama kana yace "To me yafaru da wannan yanke hukunci haka? An san aure abune mai rai wata kila karshen rayuwar sa kenan, shikuma cikin taya akayi yazamo ba naka ba tana da wani mijin bayan kaine??". Abba yafaɗa yana duban sa dason jin ba'asi dan shi kan sa yashiga ɗimuwa matuka... Kafafun sa ya tanƙwashe kana yayi kasa da kansa yace "Kayi hakuri Abba da abun da zan faɗa". da sauri na ɗago kai na yayin da naji kukan ya tsaya cak na zuba masa ido babu ko kiftawa. sai ya kuma yin kasa da kansa kana yacigaba da faɗin "Lokacin da nayi tafi naje nayi wata 1 ranar da na bar garin nan tana cikin yanayin rashin sarki,ranar da na dawo kuma na tadda ta bata da lafiya bayan da na kai ta asibiti kuma likita ya tabbatar da tana ɗauke da cikin wata ɗaya gatanan kuma ita shai da ce". Yafaɗa yana nuna Ni da hannu. Salati goggo Hauwa ta farka tace "Amma lallai SALEEM a gaishe ka sabo da haka zakace ka haramta kan ka da ita sannan kuma ciki ba naka ba? zancen banza kenan mata nawa suke da ciki kuma suna jinin al'ada ai ba akan ta aka soma ba in ba ka sani ba kasani". Maganar sa ce yasa goggo Hauwa yin shiru da nata maganar cikin ɗinbin mamaki kowa ke kallon sa yayin da shiko ya karkata hankalin sa gurin Abba da son bashi amsar tambayar da yakuma yi mishi yanzu kan cewa da yayi mishi "Dalilin ka kenan?". kan sa ya girgiza kana yace "Bayan tafiya ta akwai wani wan da yake zuwa gurin ta ɗazu ma ai katan gida na suka tabbatar min da haka". wani irin zabura su Ummi suka yi suka haɗa baki wajen cewa "Wani yake zuwa gurin ta??". Abba kam hular kansa ya cire yashiga yin fifita da shi,niko ido na daɗa kura masa kamar tv... Zaman sa ya gyara kana yasoma sanar musu duk abun da baba Mai gadi da Habu mai shara da Sani direver suka sanar masa, kana ya ɗaura da ganin da Na'ima tace tayi mana a kan gado da wan da Habu shima yace yagani. salati parlour'n ya kaure da shi tuni hawaye yashiga wanke fuskar Ummi, cikin takai ci Abba ya dube ni yana faɗin "Abun da zaki saka mana da shi kenan ki ɓata mana family kin tozarta shi tozarci mafi muni me kika nema kika rasa a rayu HAMDAH me muka gaza miki wacce gatace bamu baki ba sakayyar da zaki yi mana kenan!". kai narika girgizawa hawaye na zuba a idona na buɗe baki zanyi magana Abba ya daka min tsawa. kana ya dubi Ya SALEEM yace "Tashi ka kaje hukuncin da ka yanke shine dai-dai ta haramta a gare ka kuwa tabbas". a sannu ya mike yafita da sauri na mike tsaye kamar mai tashin aljanu na bi bayan sa kafin na iso shi har ya isa farfajiyar gida da gudu nasha gaban san sa na ruko hannunsa na ɗaura kan cikina cikin muryar kuka da fizgar numfashi na da nake ji kamar zai ɗauke, ina kallon fuskarsa nace "Ya SALEEM Ya SALEEM wlh abun da ke cikin kinan nan naka ne kai ne uban sa, wlh babu wani na mijin da ya taɓa rike koda bakin mayafi nane bare har ya sanni ƴa mace bayan kai Ya SALEEM ɗan kane cikin kane wlh babu wani wan da yake zuwa guri na". fizge hannunsa yayi kana ya dube ni da kyau yace "Kada ki sake dan ganta abun da ke cikin ki da Ni ni ba uban sa bane, ke kinsan uban sa ai jeki haifa ki kai masa abunsa in yaso ki kashe shi tun a ciki tun kafin ya fito duniya a san halin da kike ciki, asan wacece ke mutum a fuska kawai, In dai irin wannan ɗan ne zai zamo nawa har abada bana so!". yana kaiwa nan ya juya yashige motar sa yafice a gidan.. Dur kushewa nayi a gurin ina wani irin kuka mai tsuma rai, na daɗe durkushe jin jiri na fisgata na mike da kyar na koma parlour in da su Ummi suke har lokacin Ummi na hawaye sai dai ta kasa furta ko da kalma ɗaya ce, goggo Hauwa da Aunty Halima sunyi jugum. ina saka kafata cikin parlour'n Abba ya takatar da ni da faɗin "Kada ki sake ki tako cikin parlour'n nan maza ki tafi kiyi nesa da mu domin zama da irin ki acikin family tamkar rugujewar ahali ce, kisani idan zuciya ta tabuga to kece sila kuma bazan taɓa yafe miki ba,bana kaunar nakuma buɗe idanuna na ganki fita min a gida kitafi duk inda zakije amma ki sani ban yarda kije gidan ɗaya daga cikin dangi naba har in dangi nane fita min a gida nace!". yafaɗa cikin karaji baya nashiga ja inajin maganar Abba tamkar saukar ruwan dalma a zuciya ta. mikewa Ummi tayi hawaye taf idon ta tace "Ina zataje Abba'n Fauzan ka bata lasisin shiga duniya kenan? bata da in da yafi nan in kuma kace ta tafi to sai dai mutafi tare". Ummi ta nufo ni tana cigaba da faɗin "Ɗiyar ka mace zaka jefawa duniya sai dai in mutafi tare". cikin fushi Abba yace "Fatima idan kika fita daga cikin parlour'n nan to ki tabbata nayafe ki". ido na waro cikin tsananin tashin hankali nashiga girgiza kai da karfi nace "Ummi dan Allah dan Allah karki fita Ummi ki koma na rokeki Abba kayi hakuri ni zan tafi". ganin tana ta daɗa matsoni yasani tahowa da gudu na rungume ta cikin muryar kuka nacigaba da faɗin "Ummi ki koma dan Allah karki fita". sai kuma na zame jikina da sauri na saka hannuna biyu na share hawaye na nakuma kai hannu kan fuskar ta nashare mata hawaye tare da yin wani murmushi ina duban ta yayin da wasu zafafan hawaye suka zubo min nace "Ummi duk inda nake a faɗin duniyar nan ko a muce ko a raye addu'ar ki itace zata zame min garkuwa in nazamo silar fitar ki a gidan nan bazan taɓa yafewa kai na ba". Najuya na dubi su goggo Hauwa da tuni suma hawaye yagama wanke musu fuska na haɗe hannaye na biyu nace "Dan Allah goggo Hauwa Aunty Halima kada kubar Ummi na ta fita dan Allah". da sauri na juya nafita a cikin parlour'n na ɗau jakata dana yar dashi a tsakar gidan da sauri na nufi kofar fita ina waige ko Ummi na biyo ni. sauri na rika yi har na fita daga layin mu.......!★ Mommyn twins ce Sauri nake kamar zan tashi sama duk da nafita daga layin unguwar amma hankali na bai kwanta ba,tafiyar nake ina ta waige-waige,sai gani nake kamar Ummi zata biyo ni. tafiyar kawai nake batare da nasan in da zani ba kokuma sanin in da na nufa ba. Karar ababen hawa da naji ya karaɗe ko ta ina shine ya dawo dani cikin hayyaci na,nayi mamakin ganin in da nake Duk da kuwa tazarar dake sakanin unguwar mu da in da nake yanzu wato winte. Gefen titi na zame nashiga cikin mutanen da nagansu zazzau ne kan bence wasu ko nata harkokin gaban su.yayin da zuciya ta keta azalzala ta ji nake idan naci gaba da jan numfashi acikin garinnan tabbas zuwa anjima numfashi'n kwacewa zaiyi yatafi abun sa. maganar da naji kusa da nine yasani ɗagowa wani ɗan yuniyon ne tsaye a kanmu yana faɗin "Yauwa motar ku yanzu kam yacika kowa ya kawo kuɗin sa". gafen da nake ya kalla kana yace "Ƴan mata ke ma a wannan motar kike?". tsintar kaina nayi da gyaɗa masa kai,yace "To kawo kuɗin ki mota ta cika". idanuna na mai da kan akwatin da ke gaba na tabbas nasan bana da ko sisi dan ban fita da ko biyar daga gida ba, hasali ma babu abun da na iya ɗauka in ba wannan akwatin ba,ganin yanata amsar kuɗin mutane sai na kai hannuna kan zip ɗin bayan akwatin ina ɗan wasa da shi a raina nake faɗin "To ko ince masa yakarɓi akwatin a bakin kuɗin motar ne, Ni har da kayan cikin ma in dai zasu ɗauke Ni suraba ni da garin nan". yadda nake wasa da zip ɗin sai yana ɗan zugewa da mamaki nakurawa aljuhun jakar ido ganin bakin kuɗi ya baiyana, da sauri na idda zuge zip ɗin nazaro kuɗin ina juyashi a hannuna naira dubu biyu sabbi dar. tunanin ta yadda akayi kuɗin yashigo cikin a kwatin nake, nan take na tuno lokacin rasuwar Inna ina zaune a cikin bedroom ɗin Ummi taciro kuɗi cikin wardrobe zatayi aika kasuwa daga cikin kuɗaɗen dubu biyu suka zubo,nakwashe ina mika mata tafita da sauri tana faɗin na ajiye bari tazo,a lokacin kuwa kasan cewar ina zaune ne kusa da akwatin sai naja zip ɗin a kwatin nasaka ciki kan cewar in tashigo zan cire na bata,gaba ɗaya nagama mance wa a she dai ban bata ba.. Numfashi na sauke a hankali na furta "Alhamdulillah". dai-dai lokacin kuwa ɗan yuniyon ɗin yake faɗin "Kawo nake". duka kuɗin na mika masa sai naga ya zare dubu ɗaya yakai hannu aljuhu yazaro ɗari biyu sai ya haɗa da dubu ɗayan nan ya mika min dubu ɗaya da ɗari biyu kenan. karɓa nayi ina juya kuɗin a hannuna "Wato kuɗin motar garin da zasu ɗari takwas kenan?". nayi tan bayar a raina, ganin duk wan da yabada kuɗi sai ya shige cikin motar dake gaban mu sai nima na mike nashige cikin motar ina rungume da akwatina. Ina alla-alla motar ta tashi duk da kuwa bansan motar wani gari zata ba ban kuma da mu da duk inda zaije ba ni dai burina nafita a cikin garin nan, bana kaunar na buɗe idanuna nakuma ganina cikin garin bana kaunar narika shakar iskar garin naji na tsani garin gaba ɗayan ta. numfashi na sauke tare da yin hamdala lokacin da motar ta hau kan titin taɗau hanyar fita daga cikin garin......★ ★★★ A nan cikin garin Bauchi kuwa, kan kace me labarin abun da ya faru yakaraɗe ƴan uwa, su Aunty Jaleela duk sun taho gidan cikin tashin hankali, Aunty Rafee'at da yanzu isowar su ita da Dr Farooq ko jiran ya dai-dai ta parking batayi ba tafito cikin tsananin tashin hankali tanufi ciki. Nan ta iske ƴan gidan dukan su zaune cikin parlour'n Ummi har da wasu ƴan uwan su, da sauri tashigo cikin parlour'n cikin muguwar tashin hankali tana faɗin "Ummi ina HAMDAH tatafi ina tasani batasan ko ina ba". Ummi da har lokacin kwalla basu dai na zuba a idon taba takai hannu ta share wasu zafafan hawaye,bata iya ce komai ba sai kwallar da ta cigaba da sharewa. cikin share kwalla goggo Hauwa tace "Tatafi bamu san in da ta tafi ba". tafaɗa tana sharce hanci. Kuka Aunty Rafee'at ta sake da karfi cikin muryar kuka sosai tace "Wlh cikin Ya SALEEM ne wlh cikin sane wlh na shaida HAMDAH bazata taɓa ai kata abun da ake zargin ta ai kata ba". da sauri tayi gun Dr Farooq da yanzu yashigo tariko hannunsa tare da faɗin "Wlh Allah cikin nan na Ya SALEEM ne Abba'n Adeel kai shai da ne". sai kuma tasaki hannunsa tayi gun goggo Hauwa tace "Goggo Hauwa kema shai da ce Ya SALEEM shine mutum na farko da ya taɓa sanin ta ɗiya mace,wlh na rantse HAMDAH bata ai kata abun da ake zargi ba wlh sharri a ke mata". takarasa maganar cikin shashsheka.. Aunty Jaleela ma nagefen Ummi takasa cewa komai sai kwallar da take ta share wa, parlour'n yayi shiru cike da jimami da sautin kukan Aunty Rafee'at......★ Ido na zuba wa hanyar da bansan na wani gari bane,duk tafiyar da motar yake gani nake baya sauri, munyi tafiyar da yakai na a wa 2,wata matar da take gefe na tabuɗe murya tace "Direba nakusa sauka ni a Narkuta zan sauka". direban ya amsa mata da to. tafiya kaɗan muka kara muka iso wani gari mai kyau da tsaruwa a dai-dai farkon shiga garin motar ta tsaya direban yace "Mun iso masu sauka a Narkuta". kasan cewar Ni ina ta bakin kofa ne yasa dole sai da na sauka kafin matar tafita, maganar direban naji a sama "Ƴan mata kema a nan zaki sauka ne". firgigit na dawo daga tunani da natafi sai kawai na sinci kai na da gyaɗa masa kai, "No wahala" yafaɗa tare da jan motar sa yayi gaba. ido na baza kan titin kowa na ta harkokin gaban sa, a sannu na masa gefe kan wani kwalbati da ya kasan ce hanyar shiga wani layi na zau na, tare da aje akwati na a gabana, yayin da masu a dai-dai ta da mashina suke ta tsayuwa suna tan bayana ina zani,wasu nace musu babu wasu kuma nayi musu shiru. najima sosai zaune a gurin. Har guri yafara rufawa yayin da ababen hawa suka yawaita kowa yana kokarin konawa gida, Ina nan zaune a kan kwalbatin, shafa cikina da naji yana ɗan motsa wa nayi yanzu kam naji ina jin yunwa akasin ɗazu da banajin ko ɗigon yunwa,duk da wunin yau bansa ko ruwa a baki na ba, dan ko breakfast banyi ba. a hankali na mike nanufi gurin wata mai sai da abinci da nake hango ta can gefen titin,kuɗi na mika mata nace "Abani abinci". sai kuma na dubawa kuɗin da nake mika mata ido da mamaki ganin naira ɗari biyu ne bayan nasan dubu ɗaya da ɗari biyu ne a hannuna, waige-waigen gefe da gefe na nayi ko dubu ɗayan yafaɗi kasa ne amma babu ko alamar sa. maganar matar naji tana faɗin "Babu abincin 200". nace "To abani drink". ta miko min gora na amsa na juya a hankali hanyar da na bi nabaza ido ko zanga kuɗin amma har na'isa in da akwatina yake babu alamar sa, kurɓa uku zuwa huɗu nayi wa drink ɗin sai naji cikina na murɗa ni sai na rufe gorar, A sannu na ɗago jin karar mota ta tsaya daf da Ni dai-dai lokacin aka zuge glass ɗin motar kasa, wani matashi ne zaune a cikin motar sai busa sigari yake,yayin da wani ke zaune a gefen sa,kai na na kawar da sauri jin hayakin sigarin yana isoni, matashin ya dubi abokin tafiyar nasa yace "Maye wannan fa ta haɗu musala zata rage mana dare sosai". Kai ya gyaɗa cikin cakewa da kayan mayen da yake ta shaka. matashin ya dubeni yace "Ya ƴanmata shigo muje mana mubaki masau ki muhuta kihuta sosai". yafaɗa yana latso laɓɓan sa, nan take maganganu Inna da tarika yimin lokacin tana kwance a gadon asibiti suka fara yimin yawo a ƙwaƙwalwa ta. rumtse idonuna nayi da karfi,sai na kuma kawar da kai na batare da nako kalle in da suke ba bare na furta wani abun. ɗayan dake zaune gefen mai zaman banza yaleko tare da ɗaga murya yace "Zazzafa ce fa nawa za'a biya ki?". nan ma banko juyo ba dan na fahimci ƴan iska ne inajin ɗayan yana faɗin "Muje gaba akwai irin su, biyu zamu ɗiba dan mu huta sosai". ɗayan kuma yace "Ta haɗu fa duk da tana cikin hijabi". "Shiyasa take taja mana aji manya masu zaren take so muje kawai". haka sukayi ta magan ganunsu sukaja motar su sukayi gaba. numfashi na sauke tare da cigaba da ambaton sunan Allah azuciya ta da nake, tafiyar su dakamar 5mn wata mota takuma tsayuwa gefe na wannan karon sai da naji gaban kirji na ya faɗi,da sauri na juyo jin muryar wan da yake cikin matar "Shigo na sauke ki a gida mana da alama dai kin rasa abun hawa ne". saurayi ne shima sai dai baiyi kama da irin waɗan can da suka wucen ba yana zaune cikin kamala, murmushi yayi min kana yakuma faɗin "Naga kin jima zaune a nan da alama dai jira kike azo daga gida a ɗauke ki in bazaki damu ba muje na sau keki a gidan". da sauri na girgiza kaina tare da faɗin "A'a Nagode kaje kawai". kai ya jinjina yadube ni da kyau tare da faɗin "To in ma bazaki shiga motata ba to ina mai baki shawara daki nimi mai abun hawa kihau ki tafi gida". murmushi yayi cikin maganar da yake kana yaci gaba "Duk wani wanda yagan ki zaune a nan to zai yi miki kallo irin kallon da waɗan can samarin da suka yi miki yanzu suka wuce,gashi dai duk mai tunani idan ya ganki bakiyi kama da irin mata masu tallen kansu ba duk da dai basa da kama, bai kamata kici gaba da jira a kan wannan hanyar ba dan yana da haɗari sosai, akwai matasa marasa ɗa'a su basa jiran amincewar mace ko kotaso ko kar taso zasu ɗauke ta da karfi su kai ta ɗaki su kulle idan suka gama kwanakin da zasu yi dake suje su yasar da ke,a irin wannan lokaci suke fitowa, babu kuma wan da ya isa ya dakatar da su domin ƴaƴan manya ne,zai fi miki kyau kitari abin hawa kitafi gida". ido na waro ina kallon sa har yakai karshen maganar yayin da tsoro ya lulluɓeni sai nashiga gyaɗa masa masa kai,shiko murmushi yakuma kana yace "Ko za'a bani aron number?". mikewa tsaye nayi cike da jin tsoron da ya ɗarsa min a zuciya na bashi baya ina ta ɗan kalle-kalle. ina jin sa yakuma maimaita tan bayar sa ganin bani da niyyar amsa shi sai yaja motar sa yayi gaba. ido na kurawa cikin layin da nake tsaye a mashigar sa, matasa da magidan ta kowa yana ta haramar tafiya masallaci sallar magriba. Da sauri na sunkuya na janyo akwati na nasoma takawa cikin layin da sauri sosai dan ba karamin tsorata nayi da jin abun da mutumin nan yafaɗa min ba,sai dai ina soma tafiyar naji cikina yayi min wani irin murɗa yayin da kai na yake mugun sara min. Na yi tafiya mai ɗan nisa sai na zauna kan dakalin kofar wani gida,tare da tafe kai na dake matsa nancin tsaramin, da hannuna ɗaya ɗaya hannun kuma na dafe cikina, tausayin kai na ya kamani sai kawai na fashe da kuka mara sauti. cikin muryar kuka nake faɗin "Wayyo Allah cikina kai na wayyo Allah na, innalillahi wa'inna'ilaihirraji'un²". wani sabon kuka ne yakuma zuwa min Allah sarki Inna banki a yanzu Allah ya ɗauki raina kamar yan da yaɗauki nata ba yafiye min wan nan rayuwar. nayima ina kuka mai matukar kona zuciya kukun da naɗau lokaci mai tsawo batare da nasan lokacin yakure har haka ba,guri yayi shiru bakajin motsin komai sai haushin karnuka da kukan wasu tsuntsaye, na rakuɓe jikin garo na cusa fuskata sakankanin cinyoyi na,an ce bacci ɓarawo ne to ni dai na tabbata duk iya satan sa bazai iya sace ni a wannan irin lokacin ba,ta ya zai sami narasar saceni bayan ina tangare a dandamalin guri wan da a iya ƴan shekaru na ban taɓa mafarkin kasan tuwa a irin hakaba,ban taɓa rayuwa cikin bakin duhu irin haka ba,ina zaune a haka gari yawaye.. nayi al'wala a panpon da ke jikin gidan da nakwana a kofar gidan nayi sallah. Koda gari yayi haske jama'a suka fara zirga-zirga a kan hanyar duk wan da yazo wucewa sai ya kalleni ganin na zame wa mutane abun kallo dai na mike naja akwati na, a sannu narika kusawa cikin unguwar haka na rika zaga cikin unguwar idan na gaji sai na sami guri na zauna in na huta sai na mike nacigaba da tafiyar da ban san in da zani ba. ranar wuni zubur nayi ina haka yunwa kishin ruwa zafin rana sune abokan rayuwata... Yau kwana na uku a kan layi nake kwana idan nayi ta yawo har dare ya riskeni sai na sami kofar wani gida na rakuɓe gefe a haka zan kwana a zaune,batun yunwa kuwa tarigada ta shiga jikina har ya zamana bana jinta sai dai cikina sai yayi ta murɗeni abun cikina yayi ta motsawa,idan naji kishin kuwa sai na bazama yawon niman kofar gida mai panpo na tara da hannuna nashi, ina sha kuwa sai nayi hawaye sabo da murɗan da cikina zai yi ta min... Zaune nake akofar wani gidan da nake tunanin a nan yau zan kwana dan yamma tayi sosai ana daf da kiran magriba, kishin ruwa ne ya dameni tun ɗazu sai dai nayi yawo a layin da nashigo yau ban sami wani gida mai panpo a kofar gidan ba,sai dai na fuskanci wannan unguwar na marasa karfi ne dan gine-ginen su ma kaɗai kagani zakasan unguwar talakawa ne. a hankali na mike na janyo akwakina nacigaba da tafiya ko zan sami ruwa dan ina jin kishin sosai, ina sharar wata kwana can na hango rijiya mutane na tsaye a kansa anata jan ruwa a cikin sa, da sauri na nufi gurin dan ruwan da nafi muradi kenan,ina isa gurin na tsaya gefe da wata ƴar dattijuwar mata nace "Dan Allah a sammin ruwa". matar ta juyo kana tace "Sha zakiyi ne?". kai na gyaɗa mata tace "Ai ho". wani ɗan kara min roba ta janyo ruwan ta zuba ciki tace "Ɗauka kisha". To nace da sauri na ɗauka nasoma sha nasha sosai sai da naji cikina ya cika sannan na aje robar tare da yi mata godiya,ta ɗau ruwan ta tatafi a hankali naji cikina na ɗan murɗa min sai dai ba kamar na duk lokacin da na sha ruwan panpo ba,a hankali nasoma tafiya naɗan yi nisa da rijiyar kaɗan sai na zauna kan wani bulo dake gefen ciyawa jin cikin bai dai na yimin murɗa ba. kai na na cusa sakankanin cinyoyi na inajin yan da cikin ke ci gaba da murɗa ni, da sauri na ɗago kai na jin abu na tafi a kafata,wani irin waro ido nayi cikin firgici da razana ganin maciji a saman kafata,cikin zafin nama na mike tsaye tare da kwalla kara na yarfe kafar da karfi macijin ya faɗi can gefe yashige cikin ciyayin dake gurin, da iya karfina nake ihun ina yarfe kafar.... "Wane ne waye a nan?". naji murya daga can ana tan baya,cigaba da tan bayar a kayi ana motsawa in da nake,niko sai ihun nake ina tsalle da yarfe ƙafan, jin an dafa kafaɗa na ana faɗin "Subhanallahi ƴar nan menene?". da sauri narike hannun matar da naji tana tan baya na da karfi cikin sananin tsoro nace "Maciji maciji maciji". nafaɗa da karfi ina cigaba da yarfe kafar, a kiɗime matar tace "Ya cije ki ko au da ma kece? me yazaunar dake a nan tun da kinsha ruwan basai kiyi azamar tafiya gida ba, kyazo gidan macizai kizau na ba'azo in da suke Bama ana tare-tare dasu acikin gida bare kinzo nan cikin su,maza zo muje a samiki magani tun kan dafin ya haura miki,wani irin zuwa unguwa ne har guri ya rufa baza'a koma gida ba". tafaɗa tana janyo hannuna,sai lokacin na gane matar itace wacce na roketa ruwa ta bani nasha ɗazun nan. ta janyo hannuna ina ɗangala kafar, tana cigaba da faɗin "Dage kiyi sauri muje tun kafin dafin ya haura miki,waɗan nan abu ai sai a hankali har gida suke shiga mana dan ma yanzu da sauki muna saka musu magani shine suke ɗan yin nesa da gidajen mu". dai-dai lokacin muka isa kofar wani gida muka shige ciki, murya ta buɗe tashiga kwaɗa sallama tare da faɗin "Zainabu zainabu matar gidan nan tana nan kuwa". wata mata tafito daga cikin ɗaki tana amsa sallamar tace "Ina nan, a'a Mama mai awara kece tafe". Matar da muke tare da ita tace "Eh,malam Musa na nan kuwa ko har yatafi masallaci?". Zainabu tace "Yana nan yanzu yake shirin fita yazaga ne, yauwa gashi ma yafito". tafaɗa tana kallon hanyar bayi, mutumin da a ka kira da malam Musa ya dube mu yana faɗin "Sannu Mama mai awara ku ne da yammacin nan". tace "Eh wlh malam Musa maciji ne ya cije ta dan Allah a sa mata magani kafin ya haura mata". ya dube ni da har lokacin ina masar kwalla yace "To subhanallah garin yaya?". Mama mai awara tace "Can gefen fadama tabi kasan kuwa kamar gidan su ne". "Kwarai kuwa Allah yasa ba mugayen bane". yafaɗa yana shige wa cikin ɗaki mama mai awara tace "Amin dai". ni dai ina nan itana masar kwalla ban iya cewa komai ba, matar malam Musa wato Zainabu tashiga tafito da taburma ta shin fiɗa tace muzauna,ba jimawa kuwa malam Musa yafi ɗauke da wata ƴar karamar jaka ya zauna gefen taburman kana yadube Ni yace na miko kafar da yaga ina ta girgiza shi,na mika masa yazuge zip ɗin jakar yaciro kayakin magungunar sa ya zaro wani farin gyale ya gyara zaman sa da kyau ya ɗaura ƙyallen saman kafata kana yaɗauko wani magani acikin kwalba yaɗan ɗiga kan ƙyallen dake kan kafar tawa. yazubawa ƙyallen ido sai kuma ya ɗago ya dube ni yace "An ya nan ne kuwa". kai na gyaɗa da sauri cikin matsar kwalla nace "Allah nan ɗin yahau". nafaɗa ina daɗa girgiza kafar dan ji nake kamar har lokacin yana kan kafata, Maganin yadaɗa ɗigawa kan gyallen kana ya dubi mama mai awara yace "Babu wani alamun dafin maciji a tare da ita gashi nan dai kina gani". sai ya mai da dubansa gare ni yace "Amma yaya kikaji da ya sare kin?". nace "Ganin sa nayi a kan kafata kawai ban san yan da akayi yahau ba". kai malam Musa ya jinjina kana yayi murmushi da faɗin "Allah ya tai make ki wata kila wucewa zaiyi ke kuma kika tsaya masa takan hanya yabi takafar ki yawuce batare da yasan kina ma gurin ba da taimakon Allah". mama mai awara ta sauke numfashi da karfi tace "To Allah ya taimaka ina gama macijiya ce dan su matan basu fiye yin saraba sai sunji matsi". Zainabu dake gefe tace "Haka ne kam Allah dai ya daɗa karewa". suka amsa da amin nidai ido naketa cirewa cike da tsoro. mama mai awara ta mike tana yiwa malam Musa godiya tayi wa zainabu sallama tayi waje nabi bayan ta. Muna fita ta dube ni tace "Allah ya kare mugayen basu cije kiba,ai wannan mai maganin har wasu garuruwa suna kawo masa jin yan sarar maciji dan shi gada yayi tun iyaye da kakani,idan maciji ya cije ka to da wannan kyallen yake gane kalar macijin da ya sare ka,sai ya baka magani,idan yasaka kyallen dai-dai in da maciji yazuba dafin sa to kyallen zai canza kala yakoma kalar jikin macijin,kinga ai yan da yaɗau ra kyallen a fari a farin sa ya ɗaga,babu rabon wahala Allah ya kare, Maza kiyi gida yanzun nan muje na nuna miki hanya mai sauki da zaki fita bakin hanya,jirani a nan na ɗauko miki jakar ki". kai kawai na gyaɗa mata yayin da naji wasu zafafan hawaye sun zubo min,yanayin yan da matar take magana yasa ni tuno da Inna ta, "Allah sarki Inna na tabbata in da kina numfashi bazan taɓa hofanta ba". Kwalla na kuma share wa lokacin da matar tadawo gaba na tana mika min a kwatina, tace "Maza ki tafi gida dare yayi ke bakya tsoron kije gida iyayen ki su miki faɗa, Allah ma ya takai ta ai da sai dai a kai ki gida da raunin maciji, yi sauri muje na nuna miki kinga har na makara markaɗen awara nafito ɗauka wa shine na jiyo kururuwar ki da yanzu na dafashi har na tsane". Duk abun da take faɗa sama-sama nake jinta wani irin kuna da raɗaɗi zuciya ta ke min sai sharar kwalla nake. muna fita gaban rijiyar nan da hannu ta nuna min hanya tace "Ki mike nan hanyar ta ɓulle har titi Allah bamu alheri". kai na gyaɗa kana a hankali nasoma tafiya,ita kuma tabi ta wani hanyar. A hankali nake tafiyar idanuna a kasa sai gani nake kamar zan ɗaura kafar kan wani macijin,duk da kuwa guri yafara yin duhu lokacin........!★ Mommyn twins ce *Masha Allah yau Allah yayi ikon sa na dawo Nagode da addu'o'in ku sosai*🥰 Ina ganin shige war matar cikin wani gida sai na rakuɓe kofar gidan da na iso yanzu, hawayen tsoro ne suka shiga zuba min a ido shike nan Ni nasan rayuwa ta ta kare yau maciji shi zai yi saniyyar barina duni,tun da kuwa garin su nazo, wani sassanyar kuka na sake mara sauti nasadakar ma kawai macijin yacije ni na mutu ko zan huta da wannan rayuwar kunci da bakin cikin. Ji nayi an gasko min toci da sauri na ɗago kai na tare da kare fuskata da hannuna sabo da hasken tocin dake haska min ido. da sauri takaraso in da nake rike da roba mai ɗauke da kullun waken awara a ciki,salati ta doka tana faɗin "Yau naga ikon Allah ƴar nan ashe baki tafi gida ba,kuma zama anan kikayi,hanyar koma wa gida ne ta ɓace miki kokuwa wani laifin kikayi kike tsoron komawa,in ba haka ba mai zaisa kiki komawa gida,ki zauna kina ta rabuɓe-rakuɓe a nan, yaran zamani ga iya laifi ga tsoron hukunci,tun da kana tsoron hukunci ai sai ka riƙa gujewa ai kata lai fi,to baki tsoron ki karawa kanki wani laifin ni sam banason yaro irin haka to menene am fanin fitowa a gidan da har zaki ki koma wa gidan ki rakuɓe a nan kinata koke-koke, to in bugun naki za ayi bagara ki koma a bige ki ya wuce miki ba, ka zauna ka karawa kanka laifi,ɗauki jakar maza kizo nan". tafaɗa tana dubana. Tana gaba ina biye da ita muka shige cikin wani ɗan ma dai-dai cin gida mai ɗauke da ɗaki ciki biyu sai kitchen da Kuma banɗaki a gefe, da kaga kidan kasan na talakawa ne sosai sai dai a tsaftace yake babu kazanta ko datti a cikin ɗan ma dai-dai cin tsakar gidan. tanuna min ɗaya daga cikin ɗakunan tace nashiga, a kasa kan taburman dake malale cikin ɗakin na zauna, babu jimawa tashigo ɗauke da kwano ta direshi gaba na tana faɗin "Ci yanzu muje na rakaki bakin titi kihau abun hawa ki koma gida, in ban da rashin hankali niyyar guduwa kikayi gaba ɗaya a gidan da kika ɗau jaka?, Akul karki kuma wan nan ba ta'adar ɗan kirki bane ci maza muje". wasu zafafan hawaye na share kana da sauri har hannuna na rawa na buɗe kwanon, tuwon jan dawa ne miyar bushashiyar kuɓaiwa,sai tashi da kamshin daddawa yake, da sauri na sa hannu na soma ci. ta fita ta kuma dawowa da kofin ruwa ta aje min,kana ta fita taje tasoma tatar kullun da ta ɗauko markaɗen sa. cin tuwan nake tamkar na sami nama,yau kwana uku da wuni ɗaya kenan rabun da nasa wani abu mai gishiri a bakina. naci tuwon sosai dan har nakusa cinye wa kana na kara da ruwa, bayana na jingina da jikin garu tare da yiwa Ubangiji godiya, a hankali narka jin murɗar da cikina keyi min yana ɗan raguwa, yayin da abun cikina da tun jiya da cikin ya murɗa ni sai shima naji ya motsa sai ya sauka kasan marana ya dunkule guri guda bai kuma motsawa ba sai yanzu naji yana ɗan motsawa da harbawa a hankali... can an jima matar taɗa go labule tace "Zo kiyi sallah kafin awara ta ta dafu sai muje na rakaki". "Tom". nace na mike nafito rike da lanta da ke cikin ɗakin kasan cewar guri yayi duhu sosai,cikin ɗar-ɗar nashiga bayin nayi sarki nafito kana nayi al'wala na koma ɗakin na gabatar da sallar isha, bayan na idar ina zaune kan sallaya tashigo,ganin da al'wala tare da ita sai na mike nabata sallayar na koma gefe. Bayan ta idar ta mike ta dube Ni tana faɗin "Taso muje ga dare nata yi ki tabbatar kin koma gida kuma kada kisa ke yin haka kinaso kishiga fushin iyaye ne fushin su musufa ce yana jefa mutum cikin halaka". wasu hawaye ne naji sun kuma zubomin "innalillahi wa'inna'ilaihirra'un". nashiga nanatawa a raina,shin nima haka zan tabbata da fushin iyaye,shin meyasa iyaye na zasuyi fushi da ni kan abun da ban ai kata ba,me yasa zasu yanke min hukunci kan abun da bana da masaniya a kansa??. maganar ta naji a sama "Yau kitashi muje kin tsaya kuka ne,ai har gida zansa mai abun hawan yakai ki, tukunna ma inane gidan ku a wani unguwa kike? dan gobe zanje na tabbatar da kin koma ko baki koma ba,kada ki sake ki kuma laifi kice zaki gudu ni bani son yaro irin haka a ina iyayen ki suke?". kuka na fashe dashi cikin muryar shashsheka nace "Ni bani da iyaye bani da komai haka zanyi tabin layi har rayuwa ta ta kare na mutu." "Zancen banza kai, to tashi ki fita min a gida kije kikare rayuwar naki acan,an ya ma ba yawon duniya kika fito ba?to ita duniya ta ishi kowa riga da wando tun da shi kika zaɓa je kibishi,tashi maza ki fita min a gida ban mayi tunanin ko wacece keba na ɗauko ki na kawo ki har cikin makwanci na,tashi-tashi maza tashi nace". tafaɗa tana nuna min kofa da babbuga hannun ta, da kyar na mike tsaye ina cigaba da kuka zuciyata nayi min wani irin mugun zafi, Na rayawa rai na tabbas idan nafi bakin titi kan kwalbatin da na zauna ranar da nashigo garin nan zan koma, har idan wani yazo yace na bishi zai bani makwanci da abin ci zan bishi, to menene am fanin rayuwa ta yanzu ratuwa ta bata da wani am fani yanzu. idanuna na rumtse da karfi jin bugun zuciya ta ya tsanan ta,a duk san da zuciya ta tafara bijiro min da irin waɗan nan tunanin sai magana ta da Inna na karshe yashiga yimin yawo cikin ƙwaƙwalwa, "kada rayuwa tajuya miki baya ki mance da uban gijin ki". ƙwaƙwalwa ta tarika amsa kuwwa da wannan kalmar, sai nashiga nanata kalmar innalillahi wa'inna'ilaihirraji'un. a hankali na kai hannu zan buɗe labulen ɗakin na fita tace "da kata,baki da iyaye ajikin bishiya kika fito?". juyowa nayi ido taf da kwalla nace "A da ina dasu ayanzu kuma sun yanke alakar da kansu,yanzu ni bani da kowa na karɓi hakan ne abisa umurnin su". ina kaiwa nan najuya ina kokarin fita tace "Zo nan kin taɓa jin yan da iyaye sukace sun yanke alakar su da ɗan da suka haifa?, in ba wani shirin kike son kullawa ba ƴar kankanuwa da ke kin iya tsara zance". wani murmushi nayi wan da yafi kukan da nake ciwo kana na dawo na zauna in da na tashi,dubana tayi da kyau kana tace "Wacece ke kuma suwaye iyayen naki? da kike shirya musu karyar sun yanke alakar ɗa da mahaifa a sakanin ku,sabo da kin kullawa ranki zaki shiga bariki, Allah shi kyau ta wannan rayuwar ba mai ɗaure wa bane zai fi miki kyau ki koma gare su ki nimi gafarar su, kirufawa kanki asiri suyi miki aure kije ɗakin auren ki asirin ki a rufe, in ban da zamani ma ai mu a da kamar ki ta isa aure, yanzu ne kawai wai sai yarin ya tagama rika a gida kafin ayi mata aure, da ɗa da dukiya ba'a yi musu mugun ta idan na barki kika fita nasan bagidan zaki koma ba dan haka bazan barki ki fita a gidan nan ba, ni da kai na zan dam kaki hannun iyayen ki, yanzu dai dare yayi ki kwana gobe idan Allah yakai mu da safe zan kai ki gida da kaina"... ni dai ban iya cewa komai ba sai sharar kwalla nake,har ta fita a ɗakin can takuma dawowa tace nataso na zo,na mike da akwatina nabi bayan ta, ɗayan ɗakin da ke jire da nata ta nuna min tace "Shiga nan ɗakin ki kwanta na gyara miki gurin kwan ciya". nace to,tana tsaye sai da taga nashi ga kafin ta wuce taje ta kulle kofar gida tadawo tashige ɗakin ta. bin ɗakin nayi da kallo,katifa ce a kasa da kaɗan yafi taburma kauri,sai wasu kayaki da kullin buhunhuna a gefe,sai dai ɗakin a share tsaf yake babu ko datti. a sannu na aje akwati na gefe na zauna kan katifar na janyo pillow da aka naɗe shi cikin tsummar zani akayi masa riga da shi,na gyara na kwanta na rufe jikina da hijabi na, numfashi na sauke lokacin da nakai hakarkari na kan shinfiɗi da sunan kwanciya,rabon da na kwanta irin haka yau kwana uku, Allah mai girma yau gani acikin wata rayuwa, saman ɗakin nabi da ido wan da kwano ne kawai rufin sa babu ko silim. Allah ke nan mai iko mai yin yan da yaso da rayuwar ɗan adam,yau nice kwance cikin ɗakin da babu gado bare wadaceccen katifa babu hasken wutan lantarki bare AC. a tunanina kwanciyar da nayi zan sami yin ramuwar baccin da ban yishi ba na kwanaki uku amma me sai naji babu ko ɗigon bacci a ido na,tunani damuwa kunci su suko addabi zuciya ta haka na ta kuka sai daf asuba bacci yasamu nasarar sace ni....★ washegari da safe ina zaune cikin ɗakin tashigo ɗauke da kwano da kofi ta dire shi gaba na, hannuna da nayi tagumi da shi na zare kana na gaishe ta ta amsa tace "Ki karya sai kiyi wanka ga ruwa can na kai miki banɗaki bari nagama suya sai mu tafi". to kawai nace. ta fita na janyo kwano da kofin ɗumamen tuwo ne da kunu mai zafi saman murfin kofin kuma awara ne da kosai suma sai turiri suke. ina gama karya wan na sako hijabi nafito, tana zaune cikin kitchen tana ta suya yayin yara suka zagaye ta sunata mika kuɗi tana zuba musu,har da matasa ma sunata shigo wa siya. a sannu na shige bayin na ɗau tsawon lokaci ina wanke jikina da nake jin nauyin datti a fatata. koda na fito daga wankan akwa tina na buɗe na ciro doguwar riga na material na saka,ina gama sa kayan nazau na kan katifa. can da jimawa ta shigo da mayafi a kan ta ta dube ni tace "Taso mu tafi yau wa menene sunan unguwar taku?". kasa nayi da kai da jikin hawaye ya cika min ido,jin ta kuma mai maita tan bayar sai na ɗago nace "Ni ba agarin nan nake ba zuwa nayi kuma ni bansan kowa a cikin garin nan ba"... Da mamaki take kallo na cike da mamaki ta zauna kan ɗaya daga cikin ɗaurin buhun dake cikin ɗakin, ta dube ni da kyau kana tace "Tanan kika ɓullo kuma?". kai na jinjina kana nace "Wlh ni ba ƴar garinnan bace,ban taɓa sanin saba". kwalla da suka zubo min na share kana nacigaba "Kada ki mai dani gidan mu domin Abba na yace in nesan ta da su idan na dawo yace bai yafe min ba, bana kuma son ta sana diyya ta naza mo silar barin Ummi na gidan mu,na gwammace nayita yawo cikin duniyar nan har rayuwa ta takare na koma ga mahaliccina". shiru nayi sakamakon muryata da ta sarke sabo da kuka. ido Mama mai awara tazuba min,niko a hankali nashiga jan shashsheka. dakyau ta zuba min ido cikin alhini tace "Ke ko ƴar nan wani irin mummunar laifi kika ai kata haka,har mahaifin ki yayi fushi da ke irin haka?". kai nashiga girgizawa cikin muryar kuka nashi faɗin "Wlh Allah ban ai kata abun da suka faɗa ba, kuma wlh Allah cikin nan nasa ne". na karasa cikin kuka sosai, cikin tsananin mamaki tamai da idanunn ta kan cikina dana ɗaura hannu kansa,kana ta mike tadawo kusa da ni ta zauna tare da jan hijabi na ta zuba wa cikina ido, kana tace "Ba shakka ga ciki nan wanene mai cikin? yanzu ƴar nan wannan abu kika ai kata akan yaya iyayen ki bazasuyi fushi dake irin haka ba ciki ciki". tafaɗa tana tafa hannu. kai nashiga girgiza wa nace "Wlh ban ai kata zina ba cikin nan na Ya SALEEM ne". hannuna ta ruko cikin rashin fahim ta tace "Waye shi ɗin ta ya akayi yayi miki ciki to in ba zina ba menene?? kiyiyo ciki a waje kice ba zina kika yi ba to menene sunan shi??". ta jero min tanbayo yin ida nunta a kai na cike da fargaba da son jin ba'asi. wasu hawaye masu zafi da kuna na share kana a sannu nashiga bata labarin rayuwa ta,tun daga san da nafara sanin koni waye, har abun da yafaru dani yafito dani daga gida har kuma yau da nake zaune a gaban ta. kuka sosai nake har numfashi na yana fizga abun da yafaru da rasuwar Inna yadawo min sabo fil a zuciya,cikin muryar shashsheka nace "Allah ka kashe ni nahuta,kaɗauki rayuwa ta ko zuciya ta zata sami sassauci!!!!". numfashi ta sauke cike da tsananin alhini da al'ajab. Tace "Akul kidai na faɗan haka babu kyau Allah yafiki son kanki, yakan jarabci mutum dan yagwada imanin sa, hakika mahai fin ki ya yanke hukunci cikin fushi sai dai duk wan da hakan yazo masa rana a saka dole yaji babu daɗe,shi kuma mijin ki ya kama ta yayi tunani ko da a ce hakan yafaru da gaske aure yabashi,amma tun da yace bai amin ce ba bai kuma karɓi cikin ba to shi kenan, ƴaƴa nawa suka rayu batare da uba ba, Allah sauke ki lafiya yataya ki rukon abun da zaki haifa,su kuma waɗan da sukayi ruwa sukayi saki wajen ganin sun ɓata aure, Allah yanuna musu buwayar sa da izzar sa na kwatar wa wanda aka zalinta hakkinsa tun anan duniya, zaki zauna tare da ni a nan har zuwa lokacin da zuciyar mahaifin ki zai sassauto daga fushin da yayi." Nan tarika yi min nasiha takuma nuna matukar tausayar ta gare ni,har sai da taga na dai na kukan. nan take faɗa min ita ɗaya ce a gidan mijinta ya rasu tun da daɗe wa, ƴaƴan ta uku sai dai tun suna kanana suka rasu dukan su. Duk da halin da nake ciki amma na tausaya mata dajin bata da ɗaya. Batabar ɗakin ba har sai da taga na dai na kukan gaba ɗaya. can an jima ta kuma dawowa tace na fito tsakar gida zama Ni kaɗai zai daɗa kara min damu wa... tun daga ranar Mama ketason gusar min da damuwa ta, sai dai banajin har na mutu damuwa da ɗacin dake raina zai yaye gaba ɗaya. Sai dai nakan yi iya bakin kokari na wajen ganin na ɓoye damuwa ta ganin tana nuna kulawa da son ganin na kwantar da hankali na,na sawa zuciya ta salama. nakan faki idon ta a duk san da zuciya ta tatuno min da abun da yafaru sai na shiga bayi nata kuka har sai naji zuciya ta taɗan sami sassauci, haka ma idan natuno da Ummi na ko wani hali take ciki yanzu,nan ma bayin nake shiga nayi kuka na. mama bata taɓa barina na nazauna a ɗaki ni kaɗai,da zarar taga nashiga ɗaki naɗan ɓata lokaci zata leko tace na fito, wani sa'in ko makota zata shiga sai tace nazo muje. idan aka ganmu tare a ka tan bayeta wacece Ni sai tace ƴar kanin tane tazo daga garin su Yola.. ....★ Da misalin ƙarfe 4 na yamma zaune muke a tsakar gida, ina surfe wa mama waken kosan gobe, Ita kuma tana wanke waken awara, yanzu tare muke yin ai kin kosai da awar duk da hanani yi datake,wani sa'in ma Ni nake soya mata tun idan naji hayaki kai na da ido na suyi ta ciwo har yanzu na saba,wani sa'in kuma ita zata rika suyan Ni kuma na rika zubawa masu siya. Juye waken mama tayi cikin robar kai markaɗe ta mike tana faɗin "Yau baza ayi awarar dare ba gaskiya jiya dukan mu bamu yi bacci da wuri ba gashi yau da safen ma bamu huta ba,yanzu daya kamata ace hutu muke gamu gaban wake,kullum ai kin kenan kuɗi kuma ba taruwa yake ba". Jinjina kai nayi Allah sarki Mama kullum haka take faɗa wai sai dai mukare a gindin wuta amma bamu aje wani ribar kirki,bayan da ribar muke ci musha da sauran bukatu. Murmushi nayi nace "Mama ayi kawai tun da an sa har Da waken yau,kuma anjima zaki ga anata shiga nima". tace "To shike nan ai badun an jikan bakam gaskiya da mun huta yau".......!★ Mommyn twins ce Tun waye war garin yau nake jin tashin zuciya da warin magani a jiki na, yau kwana huɗu kenan nake ta fama da irin wannan yanayin,sai dai nayau yafi na sauran kwanakin, shiga na bayi sau uku kenan inata wanke jikina wai ko dun zan dai jin warin da kuma tashin zuciyar, amma sai ji nake kamar karuwa yake. Sabulun da Mama ta siya min mai kamshi wan da tun ɗazu shi naketa wanke jikina da shi na kuma ɗau kawa yanzu na fito tsakar gida, yawun da ke kunshe a bakina naje can gefe na zubar, fuska na yamutsa jin zuciya ta naci gaba da tashi kamar zanyi amai, Mama dake jajjagen kayan miyar abincin rana ta dube ni da kyau tace "Ya dai HAMDAH". "Bako mai Mama". nafaɗa ina daɗa yamusa fuskar, ganin yan da nake ta zubda yawu yasa mama bani goro tace nasa a baki na zai ɗan rage min yawun. boket nakuma cikawa da ruwa na shiga bayi nayita mulke jikina da sabulun sai da na kusa karar da salun kafin na fito,bawai kodun na dai na jin abun da nake jin ba sai dai dun gajiyar da nayi. ina shiga ɗaki nayi wurgi da sabulun na sulale sakiyar ɗakin na zauna, kai na na dafe jin yadda aman ke ta kokarin tahowa,sai juya kai nake. da sauri na janyo akwati na na buɗe cikin hanzari nakifa fuskata cikin akwatin ina shaƙar ɗan guntun kamshin turaren Ya SALEEM,daya zauna ciki sabo da kayana da ke ciki sai kamshin yazauna jikin akwatin duk da na wanke kayan cikin yafi akirga amma yar yanzu akwatin yana ɗauke da ragowar kamshin, duk da bawani kamshi mai yawa bane sai naja numfashi sosai nake jiyo kamshin. A hankali narika sauke numfashi jin aman na lafawa,sai dai har lokacin ban fasa jin warin maganin ba,najima fuska ta na kife cikin akwatin,sai dai har lokacin ina jin warin maganin, a sannu na mike cike da takaici da kuma tausaya wa kai na dan nasan in kwana zanyi ina shaƙar kamshin turaren sa kaɗai bazai gusar min da abun da nake jiba, kamshin sa kamshin dake fita daga cikin jikinsa shi nake so shine kaɗai mai iya fidda ni cikin wannan hali, wasu zafafan hawaye ne suka tsiraro min kan fuska nakai hannu na share, a sannu nayi kasa da hannuna zuwa kan cikina da sai motsawa abun cikin yake na shafa, baya nayi na jingina bayana da jikin garu tare da rumtse idanuna,yayin da zuciya ta ke wani irin matsanancin zafi da kuna, idanuna nakuma rumtse wa da karfi cikin zubda kwalla da ɗacin zuciya nashiga faɗin. "Shine uban ka yace bashi bane yakore ni bayan yasan jikin sa kaɗai nake shiga na dai na jin warin magani ko tashin zuciya,yasa Abba ya koreni ya nesanta ni da Ummi na da ƴan uwa na,yace kai ba jinin sa bane kada nasake danganta ka dashi,haka zaka fito duniya baka da uba kahaɗu da hantarar mutane waɗan da zasu rika yi maka kallon shege,ina ma da ace Inna ta tana nan da idan na haife ka wa ita zan bawa, na tabbata bazata taɓa bari duniya suyi maka kallon shege ba,na tabbata soyayyar da take min bazata taɓa kin jina ba ko da ya kasan ce shegen ne, na tabbata..na tabbata...na tabbata.." kukane ya kwace min sai nayi saurin kai hannuna kan baki na na toshe tare da sakin kuka mara sauti. Muryar Mama naji tana tahowa ɗakin haɗe da kiran sunana, da sauri nayi kokarin sai da kukan nashare hawaye na cikin hanzari, buɗu labule tayi tana faɗin "HAMDAH mekike yi ne acikin ɗakin tun ɗazu ko bacci kike ne??". shiru tayi da maganar nata tare da zuba min ido daga bakin kofar kana tace "Au abun da kika zauna yi kenan? har sai yaushe zaki sanya wa zuciyar ki salama HAMDAH?, ko badun ni ba kodun abun cikin ki kya fauwala wa Allah komai dan tsira da rayuwar ki wajen haihuwa,idan fa kika cigaba da sawa zuciyar ki damuwa da yawan ta tuno abun da ya faru ya kuma wuce ke zaki cutar da kanki, do min kuwa yanzu cututtuka sunyi yawa,ba a son mai lalura irin naku ta yawaita shiga damuwa,sai ya iya yin sana diyyar ta ko na abun da zata hai fa agurin haihuwa". da sauri nashiga girgiza kai cikin son ɓoye damuwa ta nace "Mama bafa kukan nake ba har yanzu Ban dai na jin aman bane,kuma yaki fitowa sai dai narika jin tashin zuciya sosai". shiru tayi idanunta a kai na kana tace "To shike nan na ɗau ka ai kukan kika shigo yi,sa kaya kizo na dama miki kudun tsami wata kila yasa ki dai na jin aman". To nace,ta saki labulen ta juya dan zuwa dama kunun. A hankali na sun kuya naɗau kaya nasoma sawa. Ina gama wa na haye kan sallaya dan dama da al'wala ta na gabarar da sallar azahar kana nafito, Na tadda har ta dama min kunun garin dawa da ruwan tsamiya sai tashi da kamshin kayan yaji yake, a gefen ta bisa taburma na zauna tamika min kofin kunun, na amsa nakai kofin bakina a sannu na soma sha, a sannu cikin ikon Allah narika jin warin maganin da nake jin nan naraguwa,ina gama shan kunun ta miko min gauta a cikin farin laida tace "Tun da goron bai miki ba ki gwada cin gautar wata kila shi ya miki, gobe Litinin idan Allah ya kai mu zaki fara zuwa awu nan cikin asibitin unguwar nan,gashi anata faɗakar wa a gidajen rediyo yakama ta kifara zuwa dan yana da amfani kwarai." kallon cikin tayi kana taci gaba da faɗin "An ya kuwa HAMDAH lissafin cikin nan dai-dai kika yi?, cikin wata huɗu kamar cikin wata shida ko bakwai,cikin fari da irin wannan girma haka kuma cikin fari bai fiye girma ba". murmushi nayi nace "Allah Mama dai-dai nake lissafin kinga lokacin da aka kai ni asibiti watan sa ɗaya ne dai-dai, yanzu kuma an kara wata uku kenan bayan wancan wata ɗayan kin ga wata huɗun kenan". baki mama tarike tace "Iye har kin rike lissafin dalla-dalla ikon Allah zamani da ƴaƴan cikin ta". dariya nayi cike dajin kunya narufe fuskata da tafin hannuna. ranar gauta da kunun tsamiya na wuni sha cikin yardar Allah kuwa naji sassaucin abun da nake ji. Washegari da sassafe ina kwance Mama tashigo ta tadani tace natashi na shirya natafi asibiti yin bukin, bayan nayi wanka na shirya tare da ita muka tafi asibitin,ita tayi ta zirga-zirga da cuku-cuku ina zaune sai dai abun da yakama dole sai nayi da kai na nake binta muje. Sai wajen karfe 1 muka gama komai har da awun, Kasan cewar yau ɗin Monday ne hakan kuwa yayi dai-dai da yau ne ranar awun masu cikin fari,dan haka ya zamo ranar zuwa awo na kenan duk bayan wata ɗaya. A gajiye muka shigo gida ga yunwa, kitchen na shiga na ɗauko kofin ragowar kunun tsamiya ta da mama ta dama min da safe kafin mutafi, na fito tsakar gida gindin ɗan bishiyan tsada da muke zama musha iska na zauna kan taburman data shin fiɗa, ita kuma ɗumamen tuwo ta zubo tazo tazau na tana ci muna ɗan taɓa hira,har ta kammala, lai dar magunguna da aka bamu a gun awu tajanyo ta fiddo da magungunar, da sauri na kawar da kai na ganin maganin kaɗai yasa naji zuciya ta yaso ma tashi, "Karbi maza ki haɗiye kin ji abun da suka ce kada ayi wasa da shan kwayar yana taimako sosai,bari ma na tashi naje na nimo miki ƴan abubuwan da suka ce kirika ci wake kam muna da shi,karɓa kisha na tashi". juyowa nayi jin abun da take faɗa ji nayi kamar na zandara ihu, maganin ta mika min tare da miko min ruwa tana cigaba da faɗin "Karɓi mana kada su sha iska". amsar maganin nayi ban da ruwan nace "Ni da kunu zan sha bazan iya sha da ruwa ba". tace "To sha dashi ɗin". da kyar na haɗiye da kunun ma jin yana kokarin dawowa da sauri naɗau agwaluma da ta siya min a asibitin naso ma tsotsa da sauri. ta mike tana faɗin "Bari naje gurin mai kayan miyar can na haɗo cefani". kai kawai na gyaɗa mata tafita. Baya na na jikina da jikin bishyar da nake zaune a gindinta,a hankali naci gaba da shan agwalumar, Ina zaune agun har ta dawo da cefane niki-niki a talakance, nayi mamakin ganin har da hanta a cikin cefanen, batare da ɓata lokaci ba ta haɗa min gwaten wake da hanta da ganyen ogu. kamar yan da ma'aikatan asibiti suka faɗa... duk bayan kwana biyu Mama zata siyo kifi ko hanta ko kwai ta sarrafa min shi, lurar da nafara yi jarin awara da kosai yafara yin kasa nasan ba komai bane ya kawo hakan sai waɗan nan kayan cime-cimen da take girka min, wani ranar da zata je yin cefanen har takai bakin kofa nabiyo ta da sauri nace "Mama ki bar kashe kuɗin nan haka kwanakin baya awara mudu huɗu ake yi kosai mudu biyu, amma yanzu mudu biyu ake yi wani sa'in ma mudu ɗaya da rabi,kosai kuwa yanzu mudu ɗaya ne,kuma fa duk wannan siyan kayan abin cin da aka faɗa a asibitin ne yake cinye kuɗin,Ni dai Allah Mama ki bar siya haka ai naci da yawa ma fiye da yan da suka faɗa tun da sunce kwai ɗaya ma naci ya wadatar,kifi kuwa ko na ɗari ne ba sai lallai an siyi hantan ba". tace "Tafi can me kika sani so kike kizo haihuwa kirasa jini sai an yi faman niman jini ko,ai waɗan nan abubuwan da kike cin sune zasu tai maka wajen kara miki jini, ko kin zubda jini gun haihuwa ma baza a sami wata matsala ba dan akwai jinin a jikin ki sosai". kai na jinjina. waje tayi tana cigaba da faɗin "Yo menene amfanin niman kuɗin da baza'a magance damuwa ba lafiya ai yafi kuɗi". juyawa nayi na koma ciki ina saka yadda zanyi na hanata kashe kuɗin nan da yawa dan yanzu jarin da muka dogara dashi ɗin ma yafara yin kasa idan ya karye gaba ɗaya wace madafar zamu dafa... Acan kasar India lokacin da Ya Masa'ud yasa mi labarin abun da ya faru,bakara min girgiza da tashin hankali ya shiga ba,cikin matukar tashin hankali yabaro kasar yatoho Nigeria,yayi kuka da hawayen sa da yazo ya iske Abba yakori HAMDAH ba'a masan in da take ba kuma yahana a nimo ta. lokacin yayi yunkurin nimota Abba yace kada ya soma,bai dai bi na Abba'n ba, ya baza cigiya cikin garin Bauchi sai dai ba'a sami wani alamar da ya nuna tana cikin garin ba. su Aunty Rafee'at sunyi yunkurin kiran su Abbu da suke can kasa mai tsarki su sanar musu, Ummi tace kada su sanar musu su barsu suyi iba dan su cikin nutsuwa da kwanciyar hankali da lumana. kullum Ummi na kan sallaya tana yiwa ɗiyar tata addu'a da fatan samin kariyar Allah agare ta aduk in da take a faɗin duniyar nan.... ....★ After 1 month Yau da wuri na dawo daga awu dan da sassafe Mama ta tashe ni na shirya ta rakani har cikin asibitin kafin ta dawo, lokacin da muka isa asibitin mutum uku na samu a gabana. na shigo gida na tadda Mama tana ta suyan awara masu siya sun zagaye ta, ɗaki na wuce na tuɓe hijabi na na aje laidar agwaluma da na siya da ɗarin da Mama ta bani tace ko zan ga wani abun da nake so na siya, kana nafito. in da take na isa nayi mata sannu da ai ki tace "Har kin dawo da wuri haka an yi miki awun kuwa?". nace "Eh ai yau mutum uku ne a gaba na". tace "Ai yafi kaje da wuri ka dawo da wuri wani watan ma da wuri zamu tafi". kofin kunun tsamiya mai ɗumi ta miko min da alama bata jima da dama shiba, ta tsamo kosai cikin mai tazuba cikin kwano shima ta miko min na amsa, zan zauna kan kujera tace "A'a ɗauko taburma ki shin fiɗa kimike kafafun ki". nace to. Ko da tagama suya kan taburman da na shimfiɗa tazo ta zauna cinikin da tayi ta zube su kasa muka soma kirgawa,muka cire kuɗin komai da akayi amfani da shi, cikin murnar ganin yau an sami riba har dubu ɗaya da ɗari biyar baki na washe nace "Kai gaskiya yau kam an sami riba har dubu da ɗari biyar". murmushi tayi tace "Ai kam yau alhamdulillah bari na fita nayiyo mana cefani". da sauri nace "Yauwa Mama yau ni dai bana jin sha'awar hantar nan gara kifi ma kiyi mana irin miyar waken suyar da ranar kika yi manan nan sai asa kifin kawai a ciki". Nafaɗi hakan ne dan nasan tana fita ribar da aka samun zai kare wajen yin cefanen girkin da take yi min wai na karin jini har sai ta taɓa uwar kuɗin ma. tace "To shike nan sai ayi shi tun da kina so". sallamar da akayi ne yasa mu ɗagowa dukan mu, Wani saurayi ne mai suna Sagir dake layin unguwar, kusan kullum sai ya shigo siyan awara, da ai kowa yake a siya masa amma yanzu da kansa yake shiga cikin gidan ya siya, idan ya shigo yarika bina da kallo kenan idan na gana haka sai na shige ɗaki. karaso wa in da muke yayi yana faɗin "Mama ban shigo da wuri ba Allah dai yasa an ajiye min". murmushi Mama tayi tace "Ai kuwa yau Sagiru gaba ɗaya na mance da ma HAMDAH ce ke tuna min waɗan da ake ajiye musu ai kuwa yau ban ajiye wa kowa ba na man ce gaba ɗaya dan ita mai tunin bata nan bata jima da shigo wa ba, Sai dai kuyi hakuri sai na dare kenan". tsayuwar sa ya gyara tare da dubana yace "Shine yau baki tunawa Mama ba ai da kafin ki fita kin tuna mata da ta ajiye min kinga dai yanzu laifin kine". "Laifi na kuma?". yace "Eh ai kece baki tuna mata ba". Mama tace "To an jima kam zata yi min tuni sai na ajiye maka". yace "Yauwa to Allah yakai mu". Sai kuma ya ɗan sosai bayar keyan sa ya dube ni kana ya mai da duban sa kan Mama yace "Mama zaki bani wan nan ɗiyar taki mai rashin tunin nan". da sauri na ɗago jin abun da yafaɗa, Mama ko cewa tayi "Wa wai HAMDAH kake faɗa?". tafaɗa tana duban mu duka da shi. yace "Eh ita" Mama tayi murmushi tare da faɗin "To ai matar aure ce kai baka ganta da ciki ba haihuwa tazo dan mijin ta soja ne kaga bazai yiwu ta haihu a can ba shiyasa tazo gida". Ido ya waro tare da buɗe baki da mamaki yakai hannu yarufe bakin yana faɗin "Matar soja Innalillahi wlh ban taɓa luraba sai yau duk shigo war da nake,wai Allah ya rufa min asiri da kafata ta ɓalle sabo da sallen kwaɗo inayi ana zuba min bulala,a gafar ceni wlh rashin sani ne ki tai make Ni kada ki faɗawa yallaɓoi, wlh Ni sai yau naga cikin ni duk gani na da ita ban taɓa lura da cikin ba". yakarashe maganar yana dubana da haɗe hannayen sa guri guda alamun roko. Murmushi nayi dan kullum idan ya shigo da hijabi a jikina kuma azaune yake sami na,nasan shi yasa bazai ga cikin ba. yace "Um bari na tafi wata kila ma tsautsayin wahala ne yashi go da ni,amma da zanyi ido biyu da jarumin sojan nan da na jinjina masa dan ya iya zaɓe kwarai,ko da zai sani sallen kwaɗo sau goma sabo da na tayashi murna". Mama tace "Ah to gara dai ka tafi". "Ai natafi ma". yayi waje yana dariya....★ A can cikin garin birnin Bauchi'n Yakubu kuwa, A halin ABDULLAHI TURAKI na hango motocin su suna fitowa daga cikin airport,motocine guda uku suke tafiya a jere, cikin mota na biyu wan da yakasan ce shine na tsakiya a ciki na hango su Abbu da Mamie, fuskokin su ɗauke da farin cikin ganin su a kasar su kuma garin su........!★ Mommyn twins ce Cike parlour'n yake tam da ƴan uwa da abokan arziki, kowa sai juya tsara bar da aka basa yake cike da jin daɗi. Mamie bin cikin parlour'n da mutanen cikin tayi da kallo a karo na ba adadi, yau kwana biyu ke nan da dawowar su amma bataga HAMDAH acikin masu zuwa yi musu sannu da dawowa ba,ko a airport kuwa da a kaje tarar su ba ta cikin waɗan da suka je tarar tasu,bata kawo komai a ranta ba dan tasan iyanzu kam cikin yakara girma ko shi zai hanata,sin tiri kan hanya. Bayan sallar Isha Ya SALEEM yashigo cikin bedroom ɗin Mamie tana zaune tana warewa ƴan uwan ta na kan gari waɗan da bata basu tsaraba, a hankali yakara so cikin ɗakin yazau na kan kujerar da ke cikin ɗakin tare da gai da Mamie, ta amsa tana faɗin "Har yanzu baka tafi gida ba". cikin yana yin nan nasa kamar an sashi dole yin maganar ko kuma mai jin bacci yace "Eh yanzu zan tafi na shigo nayi miki sallama ne". tace "Gara kam ka tafi yanzu haka HAMDAH na can tsoro duk ya ishe ta ga Halima ma naga bata koma ba tace min anan zata kwana". wani irin bugawa kirjin sa yayi da karfi jin an ambaci sunan ta. shi har ga Allah ma ya mancewa da wata mai suna HAMDAH in ba yanzu da Mamie ta faɗa ba, tun ranar da suka rabu ya goge sunan ta cikin zuciyar sa baya kaunar yaji wani ya ambaci sunan ta, sai kuwa akayi sa'a a cikin gidan sa uwar gidan tasa wato Na'ima tayi ruwa tayi saki wajen ganin babu wan da yakuma tuno ta bare har arika ambaton sunan ta,dan hakan shine kaɗai zai tai maka wajen ganin ya daɗa mancewa da ita na har abada, kamar yan da bokan ta yasar mata tatafi bazata kuma waigowa ba sai dai ma takuma yin nisa da su. yanzu kuma ba wani zuwa family House ɗin su yake sosai ba,kuma ko da yaje ɗin ma gaisu wa ce kaɗai suke yi yatafi. da karfi-karfi haka zuciyar sa ke bugawa,har sai da yakai hannu ya dafe dai-dai saitin kirjin sa. Mamie ta janyo wani ɗan madaidaiciya akwati tabuɗe, dogayen riguna ne da gyale da sauran su zafafa sai gefen cikin akwatin kayan baby ne wanda mace da na miji zasu iya sawa. murmushi tayi tare da faɗin "Ga tsara bar ta dana mai gidan dan Ni wa mai gida na tsiya bawa kishiya ba,Abbu ne yayi wahalar siyowa kishiya". tayi maganar fuska ɗauke da murmushi cike da so da kaunar jikan ta da take saran fitowar sa duniya ko mace ko na miji. ta cigaba da faɗin "Da zan baka kakai mata amma dai bari na bari idan tazo sai ta haɗa dana gun Abbu'n ku ta tafi da shi tun da shi har yanzu bai buɗe jakar saba". Har lokacin hannunsa na dafe kan kirjin sa a hankali ya mike,batare da yace komai ba yafita, bayan sa Mamie tabi da kallo bata kawo komai a ranta ba dan tasan halin ɗan nata sarai miskilanci a jinin sa yake. yana dai-dai ta zaman sa cikin mota yaja gajeren tsaki jin har lokacin zuciyar sa bata fasa bugawa ba,a haka ya koma gida.. Washegari Mamie tayi ta zuba ido ganin zuwan HAMDAH amma shiru har yamma. A ɓangaren Abbu ma ranar sai da ya tanbayi Mamie wai shin HAMDAH tazo ta karɓi tsara bar tane bata karɓi na amaryar sa ba. Nan Mamie ke ce masa ai ko sannu da dawowa bata zo musu ba amma dai tasan jikin ne yasoma nauyi... Bayan sallar magriba, da sauri Masa'ud yabi bayan Abbu suka shiga gida tare, a parlour suka zauna in da suka tadda Mamie nan zaune,zama Masa'ud ya gyara dan yau yasha alwashin faɗa wa su Abbu abinda ke faruwa duk da Ummi tace kada wani ya sanar musu sai sun daɗa hutawa sosai. a cewar sa wani hutu yarage musu bayan ƴar uwar su ba a san halin da take ciki ba. "Abbu Mamie". Masa'ud ya kira sunan su yana duban su,a kusan tare suka amsa yayin da suka mai da hankalin su kan shi. Zaman sa ya daɗa gyarawa kana ya nisa yasoma magana, "Abbu kunsan abun da ke faruwa kuwa?". A tare suka haɗa baki wajen cewa "Meke faruwa?". "Assalamualaikum" gaba ɗayan su suka juyo jin muryar Aunty Rafee'at tana sallama,suka amsa mata,ta karaso ciki ta sami guri ta zauna tare da gaishe su in da Masa'ud ya gai data. Mamie tace "Unguwar dare bakya bari gari ya waye ba". Hmm. kawai tace dan batajin abun da ke tafi da ita zata iya barin sa sai gobe, kwanaki arba'in da suka shuɗe tayi sune cikin kunci da tashin hankali, Dr Farooq ma yayi-yayi da ita kan tabari gari yawaye tace a'a yau kam bazata bari maganar yakuma kwana ba,a son ta ma tun ranar da suka dawo Nigeria taso faɗa musu Ummi ce ta hana ta,tun da har yau sun yi kwana uku da dawowa bataga amfanin rashin faɗa musun ba gara su ma susanin. Masa'ud na ganin yanayin ta yasan abun da yazo faɗawa su Abbu shi ya kawo ta, yace "Aunty Rafee'at yanzu da ma zan faɗa wa su Abbu kenan". da mamaki iyayen nasu ke kallon su Mamie da tun ɗazu da Masa'ud yace sunsan abun da ke faruwa taji gaban kirjin ta ya yanke. tace "Wai me ke faruwa ne kam?". tayi tambayar cikin yanayin fara shiga damuwa da fargaba. A sannu Aunty Rafee'at tashiga basu labarin abun da ya faru tun daga farko har da korar da Abba yayi wa HAMDAH. Kamar a mafarki haka suke jin zancen nata, Mamie kam salati tashiga rafkawa tana tafa hannu yayin da hawaye yafara sauka a idon ta, Cikin sananin tashin hankali da kunar rai Abbu yaɗaga wayar sa yakira Abba batare da ya amsa sallamar da yake masa ba yace yazo yan zunnan, yana kashewa yakira lambar Ya SALEEM, a ɓangaren Ya SALEEM ɗin kuwa yana zaune cikin bedroom ɗin sa Na'ima na gefen sa like da shi, ganin mai kiran nasa a irin wannan lokacin sai da ta ɗan girgiza, yana ɗaga kiran yace "Duk abun da kake kabari kazo yanzu ina niman ka". Abbu ya faɗa cikin fusatacciyar murya, da sauri YA SALEEM ya mike ya ɗau makullin motar sa yafita, A ɓangaren Na'ima kuwa kasa zaune tayi tarika zagawa cikin ɗakin dan duk abin da Abbu yafaɗa taji, tsoron ta ɗaya kada akan maganar yarin yar nan Abbu yayi masa irin wannan kiran, "Cabɗi jan lallai kuwa da sakel". tafaɗa a fili. Cikin gaggawa Abba ya iso sashin wan nasa do min amsa kiran sa, Abbu ko zama bai bari Abbu yayi ba ya shiga nuna sa da yatsa yana faɗin "Me ka ai kata kenan me kayi kenan Idris?? da hankalin ka da girman ka da tunanin ka zaka yanke mata irin wannan hukuncin, menene amfani da ribar yin hakan ka jefata duniya da kan ka, akan wani dalilin ka mara tushe da asali, wani gurin da yafi nan ka bata acan ɗin da ka turatan?, wani irin rashin imani ne hakan kai kana kwance a makwanci mai kyau kaci mai kyau kasha mai kyau ita tana can awani duniyar da kai kan ka baka sani ba,baka kuma damu da duk halin da zata shiga ba,a kan dalilin da baka da tabbacin sa!!". Sosai Abbu ke yiwa Abba faɗa tamkar zai rufe shi da duka cikin tsananin ɓacin rai. Ya SALEEM da yanzu shigo warsa ganin yan da Abbu keyiwa Abba yasa shi karaso wa cikin parlour'n jiki a sanyaye, da sauri Mamie da tunɗazu take ta sharar kwalla tamike tashi dukan kafaɗar sa tana faɗin "Yanzu a bun da ka ai kata ke nan SALEEM abun da ka ai kata kenan kai ɗin ka kamata da kan ka da wani acikin gidan kan? shine har zaka sake ta? shekaran ta nawa a cikin gidan sai yanzu zata kawo wani cikin gidan". cikin muryar kuka sosai take maganar tana dukan kafaɗar sa. hayaniyar da Ummi taji nafita sosai cikin side ɗin Mamie yasata fita da sauri tanufi side ɗin dan ganin meke faruwa haka a cikin daren nan, a tsakar gida ta haɗu da su goggo Hauwa da Aunty Halima suma jin hayaniyar ce tafito dasu daga sashin Inna da sukayi masau ki can,da sauri sukayi cikin side ɗin hankali tashe jiyo muryar Mamie tana magana cikin muryar kuka. Suna shiga da sauri Ummi tayi gun Mamie daketa bugun kafaɗar SALEEM shi ko na tsaye ya dukar da kan sa kasa, hannu Mamie Ummi tarike tana faɗin "A'a Mamie'n Nusaiba menene haka me yasa hakan?". Mamie tace "Kyale ni Ummi'n Fauzan idan baije yanemo taba bazan taɓa yafe masa ba,a ina ka ganta da wani kataɓa kamata tana cin amanar auren ka ko ta hanyar magana da wani ko a waya ce??!, kyale ni Ummi'n Fauzan sai ya faɗa min yaushe yataɓa kamata tana cin amanar auren sa". sakin hannunta Ummi tayi kamo na Ya SALEEM da kansa ke sun kuye har lokacin yana jin zuciyar sa nawani irin tafarfasa, ta jashi gefe. su goggo Hauwa kam tsayuwa sukayi suna kallon yan da Abbu ke yiwa Abba faɗa kamar zai rufe shi da duka. Rai ɓace Abbu ya juyo gun Ya SALEEM yana wasa masa wani irin mugun kallo, ganin haka yasa Ummi haɗe hannayen ta biyu tace "Dan Allah Yaya..." hannu ya ɗaga mata batare da ya bari ta faɗi abun da zatace ba cikin fusatacciyar murya ya dubi Ya SALEEM yace "Kai ka ɗaura wa kanka aure da ita da zaka kwance? yau nayi da nasanin haɗaka aure da ita nayi nadamar abun da nafaɗawa mahaifiya ta cewa kai zaka rike mata jika da gaskiya da amana, yau nayi nadamar faɗar hakan nayi nadamar saurin yar da da hankalin ka da nayi, da nasani da tun wancan lokacin nacikawa Inna burinta na haɗa auren HAMDAH da Masa'ud, ban yi tunanin kiyayyar da kake mata yakai nan ba, bayan ka saketa kakuma bita da mummunar kazafi!!". rumtse idanunsa yayi yana jin kansa naci gaba da yi masa mugun sara zuciyar sa na tafarfasa yana jin maganganun iyayen nasa tamkar saukar aradu. Abbu yaci gaba "Ka kira ma ai katan gidan ka da duk wani mai hannu a kan maganar yanzu-yanzun nan suzo ina neman su!!!". yakarashe maganar cikin tsawa da karaji sosai.. A can cikin gidan SALEEM kuwa lokacin da sakon kiran Abbu ya'isa gare su wasu daga cikin ma'aikatan gidan da ka gansu kasan suna cikin yanayin tsoro da fargaba,dajin kira kai tsaye daga sama. A ɓangaren Na'ima kuwa duk da itama tarazana da jin kiran,sai dai tasan bokan ta bazai barta a rana ba. batare da ɓata lokaci ba suka nufi gidan su Abbu, in da Na'ima da baba mai gadi Sani direba Habu mai shara,suka taho a mota guda,sauran ma ai katan kuma suma a mota guda... Acikin parlour'n Mamie suka tadda kaf ƴan gidan anyi jugum-jugum,suna shigowa Aunty Rafee'at tashiga ai kawa Na'ima harara cikin tsananin tsanar matar,a gefe kusa da Ya SALEEM Na'ima ta zauna,in da sauran ma ai katan suka zazzauna a kasa tare da soma gai da su Abbu, Ummi da goggo Hauwa da Aunty Halima ne kaɗai suka amsa musu. gyaran murya Abbu yayi ya dubesu da ɗaɗɗaya da kyau kana yaso ma magana "A cikin ku su wane ne suka ce sun ga HAMDAH da wani acikin ɗakin kwanan ta har kuma suka bada tabbacin sun gansu a makwanci ɗaya??". kallon-kallo Na'ima da baba mai gadi Sani Habu suka shiga yi. yayin da hankalin mutanen cikin parlour'n yadawo kansu tun da kowa yasan cewa sune suka bada tabbacin sun gansu da idanunsu. Ummi kam kanta ta sunkuyar jiki a sanyaye tana jin kunnuwan ta suna yi mata nauyi da sake jin abun da ɗiyar ta ta ai kata... Baba mai gadi ya rusanar da kai kasa kana yace "Gamunan Alhaji, ni da Habu da Sani sai kuma Hajiya Na'ima". yafaɗa yana nuna ko wannensu da hannu kana yaci gaba "Ranar da oga SALEEM yayi tafiyar da yaje yayi wata guda a ranar mutumin yafara zuwa". nan ya zaiyana bayani kamar yan da yafaɗa wa Ya SALEEM a wancan lokacin. Ido Abbu yazuba masa da kyau yana sauraren sa yayin da jikin sa yaɗan yi sanyi dajin maganar daga bakin baba mai gadi, baba mai gadi dattijo ne dan ya girmewa su Abbu'n nesa ba kusa ba. Habu da Sani suma sukayi bayani da bada tabbacin ganin su kamar yadda suka faɗa wa SALEEM, kana daga bisani Na'ima ta ɗaura, tun da Na'ima ta fara magana Aunty Rafee'at ji take kamar taje ta shaketa ta mutu dan bakin ciki,cikin tsana da jin haushin ta tace "Wlh karya ne cikin Ya SALEEM ne". ganin yan da take maganar tana nuna Na'ima da yatsa kamar zata mike, Aunty Halima ta riko hannunta cikin kasa da murya tace "A'a Rafee'at zau na kawai". huci take tana ai kawa Na'ima harara. Shiru parlour'n ya ɗauko kowa da abun da yake sakawa cikin zuciyar sa, Ummi kam wasu zafafan hawaye ne suka zubo mata da sake jin abun da ƴar ta ta aikata,cikin wani sabon tashin hankalin da ta sinci kanta ciki tashiga nanata kalmar Innalillahiwa'inna'ilaihirraji'un. Ya SALEEM na zaune har lokacin bai yi magana ba sai dai bugun zuciyar sa da yakaru tamkar zai fasa kirjinsa yafito, Abbu ya sauke numfashi sannan yace "Ina da bukatar bincike akan lamarin duk da kasan cewar ku shaidu har huɗu akan lamarin, zan sako hukuma ciki tayi bincike sosai domin daɗa tabbatar da hakan, kutashi kuje gobe idan Allah ya kai mu za'a fara bincike domin zuciyoyi su dai-dai ta kan abu guda". wani irin Rasss gaban kirjin N'ima ya buga da sauri ta mike yayin da sauran suma suka mike sukayi musu sai da safe suka tafi. Abbu ya mai da hankalin sa kan Abba da Ya SALEEM sannan yace "Gobe nakeson ganin HAMDAH cikin gidan nan". yana kai wa nan yamike yayi cikin bedroom ɗin sa.... Hankali tashe Na'ima takoma gida hankalin ta bai kuma mummunar tashi ba sai da ta sami labarin cewa Abbu yace anemo HAMDAH, washegari ana idar da sallar asuba Na'ima ta fita tanufi gidan bokan ta, hankali tashe tafito daga motar ta tatube takalmin ta tanufi bukkan malam na kan tudu, yana zaune gaban kayan tsafin sa ta zube gaban sa tana sauke numfashi kamar wacce tayi tsare, cikin sauke numfarfashi tace "Boka akwai matsala". Dariya ya sheke da shi, itako cikin tashin hankali da rawar jiki ta cigaba da faɗin "Boka komai ya kwaɓe iyayen sa sun dawo mahaifinsa yace yau zai faɗaɗa bincike akan lamarin kuma yace hukuma zai sa suyi bincike akai, sannan yace aje a nemo ta a duk inda take, boka ka taimake Ni kamar yadda kasaba tai makona". kai ya jinjina kana yaɗauki wani ɗan karamin tandu da zare mai kauri yace "Za'a rufa musu baki bazasu kara yin ma maganar ba daga yau,zasu mance da batun kuma koda sun tuno ta, baza su iya yin komai akai ba". dariya yakuma ke cewa da shi yace "Haka ya miki?" da sauri tashiga gyaɗa kai tare da faɗin "Yayi sosai ma Nagode kwarai malam ai Ni kagama min komai a rayuwa"... Wani bakin ruwa ya zuba cikin ɗan karamin tandun nan sannan ya shiga zagaye bakin tandun da zare mai kaurin nan, har sai da ya mamaye bakin tandun da zaren yarufe shi ruf, kana ya jefa shi cikin tukunyar tsafin sa,yadube ta yace "An gama". godiya tashiga zuba masa kana tabuɗe jakar ta taɗibo kuɗin da batasan adadin su ba ta zubesu a gaban sa ta hayo motar ta takoma gida... Tayi ta suba idon ganin hukuma masu bincike shiru har yamma, har dare tana baza kunne kuma jin wata magana nan ma shiru, wasa-wasa aka shari kwana uku babu wani labari, dariya tashe ke dashi tare da buga cinya tana hakimce a bakin gadon ta, "Ɗa ɗan ku haka gida ma nasa, kuma na haramta wa ƴarku do min ni kaɗai kuka haifa min shi". tayi maganar cikin nuna isa tamkar da wani cikin ɗakin.. A ɓangaren Abbu kuwa a cikin zuciyar sa yanajin son yayi bincike kamar yadda yafaɗa haka kawai kuma sai yaji yakasa ai watar da hakan,a ɓangaren Mamie ma haka abun yake tanajin abun a ranta sai dai bata iya furtashi a baki .......!★ Mommyn twins ce Haka rayuwa yaci gaba da tafiya, kamar yadda kuka sani yanzu rayuwar tafiya kawai take,dare babu wuyan yayi haka gari bawuyan ya waye,koda gudun da kwana da yini suke ya'ishi ɗan adam yayi wa kansa hisabi, domin kuwa rayuwar mu tafiya kawai take yanzu...★ haka naka narika rainon cikin Mama tana iya bakin kokarin ta wajen kula da Ni da abun da ke cikina, lokacin da cikin yakai wata bakwai da watan yakai karshe, tun daga lokacin nazamo abun tausayi bana iya yin bacci dazarar dare yayi to bacci yakaura ce min ina so nayi amma babu hali,dazaran na kwanta sai naji kamar na kwanta kan kaya duk inda na juya babu daɗi, ban isa na kwanta ba sai dai na jingina da jikin garu kokuma na zauna sakankanin buhuhuna natokare gefe da gefe na,a haka zan samu naɗanyi gyangyaɗi, cikin ga masifar nauyi da girma ni kaina yanzu ina ganin girman cikin da Mama take faɗa. a haka har watan yakare,ina cikin wannan halin... Cikin ikon Allah yau cikin yashiga wata 8 dai-dai. kamar ko wani lokacin zuwa awo na idan yayi da sassafe Mama ke tashi na mutafi yauma hakan take, kasan cewar natafi da wuri da wuri nafito daga asibitin, da kyar nake ɗaga kafata nanufi gida, ina tafiyar ina hutawa har na isa gidan. azaune na iske Mama kan kujera ƴar tsuguno,tana ganina tamike taɗau taburma tashin fiɗa tana faɗin "Zauna ki mike kafafun ki sannu kinji". Kai na gyaɗa nazauna ina sauke numfashi,cikin tausaya wa ta dubi cikin ta cigaba da faɗin "Kai wannan ciki naga alama shi yake janki Ni sai gani nake kamar ma cikin yafi karfin ki". kallon cikin nayi tare da yin murmushi, tamike ta kawo min abinci da kunun tsamiya tace "Ci sai ki kwan ta ko zaki samu ki ɗan yi bacci". nace To... Ina gama ci Mama tamike tace bari ta kawo min pillow na mike a nan dan yafi iska, nace to. tana shiga ɗaki aka fara kwaɗa sallama da karfi-karfi murya naɗaga na'am sa sallamar da nake jin sa kamar ihu acikin kunnena. mirgina wa nayi da kyar na mike nanufi kofar gida, wani katon mutum na gane a tsaye daf da kofar gidan, kallon mutumin nayi dan na gane shi ganina da shi na biyu kenan gaishe sa nayi ya amsa fuska a turnuke sannan yace "Fasuma tana ciki?". nace "Eh". fuska yadaɗa turnike wa ya turo tunbi gaba yace "Je kice mata Alhji Mamman ne yazo". nace to. najuya nako ma ciki Mama na sun kuye tana gyara min pillow da ta dauko min na karaso in da take tace "Yau wa zo ki kwanta ko Allah zai sa ki Sami bacci ko bakiyi da daddaren ba zai zo da sauki". nace "To, Mama wai Alhaji Mamman yazo". cak ta sai da hannunta daga abun da take,ido naɗan tsura mata ganin yanayin da ta shiga daga faɗa mata wan da yazo ɗin, tana sunkuye kanta a kasa bata kuma aje pillow'n dake hannunta ba. karo na uku kenan aduk san da Alhaji Mamman yazo ina lura da ita irin wannan yanayin take shiga, "Ko me yasa?". nayi tambayar azuciya ta,a sanyaye ta ɗago ta nufi ɗaki can tafito da mayafi da kuma kuɗi a hannunta, tanufi kofar gida. Daga in da nake zaune inajuyo sautin Muryar Alhaji Mamman sai dai bana fahimtar abun da yake faɗa, taɓa lokaci kafin tashigo,ido na bita da shi har takara so in da nake, kan kujera ƴar tsuguno ta zauna jiki ba kwari, tadube ni nima ita nake kallo kallo ɗaya zaka yi mata kasan cikin muguwar damuwa take, "To wanene shi?". nakuma yi tan bayar a zuciya ta, wan da bansan har ya fito ba sai da naji tace "Hmm wan mai gida nane ubansu ɗaya". da sauri na kuma duban ta taci gaba da faɗin "Shi ne mai wannan gidan zaman haya dama muke aciki, to bayan rasuwar sa sai nauyin yadawo kaina ni nake biyan kuɗin hayar to yanzu yana bina kuɗin shekara 2 ne da ban samu na biya ba shine yake ta sintirin karɓa, ƴan kuɗaɗen da suke hannuna na kai masa kafin na samu wasu na kara masa yaki karɓa, wai sai na haɗa masa duka na shekara biyun, yanzu dai na basa hakuri yatafi, to bari mu gani mu ɗan taɓa sana'ar na ɗan kwana biyu ko Allah zai za a samu ɗan wani abu sai a haɗa abashi". tau sayin Mama ya kama ni kwarai nace "Allah yasa a samu acikin satin nan ma sai a basa". tace "Amin"... Bayan sati biyu. hakan yayi dai-dai da watannen cikina 8 da sati biyu, zaune nake a ɗaki bayan na idar da sallar azahar da sauri na yunkura na mike da kyar jin fitsari ya taho min lokaci guda kamar zai fito,da sauri na fita naje bayi nayi,nayi mamakin ɗan fitsarin da nayi bana kirkiba amma nake jin sa kamar zai fito kafin na isa bayin. Na komo ɗaki ina zama bada jimawa ba nakuma jin irin fitsarin ɗazu, koda na koma bayin shima ba da yawa nayi ba,sai dai nayi irin haka har sau hudu,zuwa yanzu kam abun yafara damu na,yunkurin mikewa nake jin wani ya taho,amma nayi nayi na iya mike wan na kasa, da kyar na tattaro ragowar karfi na na yunkura zan mike, ba shiri na koma zaune da sauri jin wani irin sarawar da bayana yayi da mugun karfi. a take kuma marana shima ya amsa dayi min wani irin mummunar murɗa, sulalewa kasan ɗakin nayi nashiga murkususu. Cikin tsananin jin azaba da karfi na furta "Innalillahiwa'inna'ilaihirraji'un!". da sauri mama dake ai ki tsakar gida tashigo tun kan ta karaso take faɗin "Yaya dai lafiya HAMDAH?". cikin hanzari takaraso in da nake kwance ina juyi cikin azaba cikin tashin hankali tace "Subhalallhi yaya dai HAMDAH". kai nashiga juyawa cikin jin azaba da kyar na iya furta "Wayyo Allah bayana marana wayyo Mama zan mutu". a kiɗime ta ɗa goni ta tallafo ni jikin ta tana faɗin "Ikon Allah sannu ina ganin juyi ne dai dai lokacin haihuwa kam da saura sannu kinji".. hannunta na kankame da karfi jin marana ya kuma murɗani sai naji fitsarin nan irin naɗa zu nan da nan jikina yakama rawa nadaɗa kankame Mama da karfi nabuɗe baki zanyi magana sai naji wani ɗumi yana bin kafata, da mamaki Mama ke kallon kafata tace "Ikon Allah ga alamar haihuwa kuma tun lokaci baiyi ba". ni dai a sama nake jinta dan azabar da nake ji yanzu yafi min kama da nafitan rai duk da bansan zafin fitar raiba amma nasan babu abun da yakai shi zafi, nagama sadakarwa raina ne zai fita dan azabar da nake ciki yanzu yawuci na kwatanta shi. maganar ta nakuma ji a sama tana faɗin "Tabbas haihuwa ce an ɓata da lissafin ne dai". pillow ta janyo ta saka kai na a kai kana ta mike da sauri tafita,can an jima ta wado rike da kofi da ruwan hulba wan da ta tafasa shi ta tallafo kai na tasaka min kofin a baki tace "Sha da zafin sa in sha Allahu zai zo miki da sauki". da kyar na buɗe baki na soma sha nan take wani sabon zufa yashiga keto min.. Akai-akai tarika bani ruwan idan yaɗau sanyi sai taje ta ɗuma takuma bani nasha,zatona zan ji sauƙin kamar yadda tace amma me sai ji nake kamar ana daɗa hangizo ciwon ne, kofin tamiko min tace "Karasa wannan sai na je na karo wani in Allah ya yar da yanzu zaki warke". kuka na fashe dashi cikin muryar kuka nace "Wayyo Allah Mama Ni dai idan nasha ciwon karuwa yake daɗa yi". da sauri tace "A'a yi shiru dai na kukan ba'a yin kuka a irin wannan ciwon ai karuwa ciwon yake yi idan kace zaka yi masa kuka,ko kina so ya karu ne?". da sauri na girgiza kai tace "To in kuwa haka ne kada ma kibari wani yaji kukan ki ko Ni da nake kusa dake in kuma ba haka ba to ciwon bazai taɓa bari ba sai dai ma yakaruwa addu'a zaki rika yi da salati nima kuma zan taya ki". cikin jin tsoron abun da tafaɗa na haɗiye kukan sai juya kai nake cikin jin azaba... abu kamar wasa sai daɗa zamowa gaskiya yake,tun azahar har la'asar ina abu guda faɗar kalar azabar da nake ciki bazai misaltu ba, zuwa yanzu Mama ta fara shiga damuwa ganin an shari wasu ƴan awanni babu wani labari,ta dube ni cikin tausayawa tace bari taje gun Malam Musa ta amso min magani. tafita da sauri, batare da ɓata lokaci ba ta dawo rike da kwarya a hannunta tana kusa kan ta cikin ɗakin tayi wurgi da kwaryar da gudu takaraso in da nake durkushe sai kakkkarwa nake narike marata danake jin kamar zai fashe da karfi,sai nanata kalmar Innalillahiwa'inna'ilaihirraji'un nake. taruko ni tana faɗin "Innalillahiwa'inna'ilaihirraji'un, taso muje asibiti sannu ƴar nan daure ki mike". sai kuma ta sake ni tafita da sauri tana faɗin "Bari na taro mai abun hawa". tana fita akaci sa'a tasamu a kofar gida yasau ke wata mata ta tsai da shi takomo ciki da tai makon ta na iya mikewa tsaye a duke muka fito,muka shiga napep muka nufi asibitin danake awu, batare da ɓata lokaci ba suka karɓe ni aka shige dani ɗakin da aka tana da domin masu haihuwa. nan da nan nurse's suka fara ai kin su, sai dai har yamma labari bata sauya ba, sai gashi-gashi haihuwa zai zo sai ya tsaya duk wani iya bakin kokarin nurse's ɗin sun yi amma abun yaci tura,har aka kira sallar magriba, sukace gaskiya yafi karfin su mutafi babban asibiti. A cikin adai-daita mama narike da ni dan zuwa yanzu karfi na yakare gaba ɗaya,da kyar na buɗi baki nace "Mama ki mai dani gida kawai ni nasan mutuwa zan yi". cikin tashin hankalin da take ciki tace "Ki dai na faɗan haka HAMDAH in Sha Allahu zaki sauka lafiya da yar dar uban giji".... koda muka isa asibitin aka shiga bani tai makon gaggawa, likitoci mata uku ne a kaina biyu mata ɗaya na mini. Inaji cikin harshen turanci suke faɗin "Bazata iya haihuwa da kan ta ba dole sai an mata CS yanzu kuma batare da ɓata lokaci ba". kuka na fashe da shi ina faɗin "Wayyo Allah Inna Ummi na wayyo Allah na". rarrashi na suka shiga yi nan suka nimi ganin miji ko uba domin sa hannu kafin suyi CS ɗin, sannan kuma sai an ajiye 25k shima ɗin na siyan kayan ai kin da za'a yi amfani da sune kuma cikin gaggawa. hankalin Mama yakuma mummunar tashi,tace "Mahai finta ya rasu Mijin ta kuma baya gari amma yaba da izinin ayi mata amma dan Allah kuyi mata yanzu zanje nakawo kuɗin". Mama tafita cikin tsananin tashin hankali. Ni da kai na da naji azabar yanin ka na ɗazu nace "Dan Allah kuyi min kuraba ni da wannan cikin.....★ ★★★ 2hr ago ★★★ Bayan waɗan nan awan nin Likitoci suka sami nasarar yimin ai ki wan da duk abun da ake idanuna biyu ina kuma ji, in da suka ciro baby'n sai dai duk yan da suka so na kalli abun da na haifa fir naki dan har lokacin ina cikin jin azabar ciwo duk da kuwa allurar da akamin....!★ *Kukaran ta da hakuri🤦🏻‍♀️ ban sami damar yin editing ba* *Saura kuce yayi kaɗan😂 bari ma na fece🏃🏻‍♀️* *Nasan ki sarai Rabin jiki maman korafi Allah yasa naji wani magana sai natafi yajin ai ki*🤣 *To oga yace Saturday and Sunday lokacin sane to gashi na ɓantara muku lokacin sa🙈🤣* *Ƴan HAMDAH FANS 2 sun fiku son na adana oga*🙈😂 Hankali tashe Mama ta isa gida in da ta ajiye asusun da take tara ɗan ribar awara da kuɗin da tabawa Alhaji Mamman yaki karɓa tasaka ciki gudun kada ta kashe, ta fasa asusun hannunta na rawa tashiga kirga kuɗin data ciro cikin asusun, naira dubu shida da ɗari biyar ne kacal. cikin matukar damuwa da tashin hankali tarika juya kuɗin a hannunta wan da bai kai ko rabin kuɗin da ake bukata a asibiti ba. da sauri ta fita tashiga gidan makotan su bayan sun gai sa da Kulu mai masa Kulu tace "Gagurin zama Mama mai awara". Mama tace "A'a Kulu banga ta zama ba HAMDAH na asibiti za'a yi mata aiki da ma aron kuɗi nazo ki bani ko na masa ne dan Allah, wlh yanzu haka ni ake jira bazata iya haihuwa da kan taba dole sai amma ta aiki kuma sunce cikin gaggawa in ba haka ba za'a iya rasa aɗaya a cikin su ko ɗan ko ita,in sha Allahu zan biya ki bayan suna". "Capɗi jan". Kulu ta faɗa tana rike haɓa kana ta cigaba da faɗin "Ikon Allah haihuwar dai tazo da gardama kenan, wlh kin gan ni da mayafi a ka gidan mai shinkafa zani wlh tun shekaran jiya take tamin sintiri yau kuwa da sassafe ita ta tashe ni tun ban ɗaura kaskon suya ba yanzu haka kuɗin ta zan kai mata." cikin matukar damuwa Mama tace "Dan Allah in kina da wani kuɗin ki taimaka ki ara min kokuma ki siyi wake na kici gaba da yin awarar kafin a sallame mu". tace "Wlh sisi bani da shi in ba wannan dubun ba". taciro gudan dubu daga bakin zanin ta ta nuna mata. sannan ta cigaba da faɗin "To kikira mijin ta mana ko a dajin sambisa yake ai zai iya turo kuɗin da za'ayiwa matar sa ai ki, abu na waya yanzu kai yawaye duk duniyar da yake idan ya tura zai iso, yaushe zaki zauna baiwa kanki wuya kune irin iyayen da kuke baiwa mazajen ƴaƴan ku kofar kin yiwa matansu jinya, har yaushe zaki zauna baiwa kanki wuya bayan yana nan da ransa". da sauri Mama ta juya bata kuma cewa komai ba saboda sabar tashin hankali bata ma fahimtar me take faɗa, tana fita gidan wata dillaliya tatafi,tace tazo tasiyi katifar ta. dillaliyar tace taje zatazo gobe da safe, Mama tace "Dan Allah ki tai maka kizo muje yanzu wlh ƴata ce ke asibiti". Tare suka taho gida da dillaliyar, dillaliya ta kalli katifar da ke cikin ɗakin Mama tace "Nawa kika masa kuɗi". Mama tace "To dai kin ga katifar sabuwa ce bataji jiki ba ban jima da siyan sa ba wlh naira dubu 27 na siya amma yanzu nawa zaki siya?". dillaliya ta kuma dudduba katifar da kyau kana tace "Na siye shi dubu 8". Da sauri Mama tace "Haba ke kuwa dubu 8 gaskiya bazan sai da shi haka ba ki kara dai". fuska matar ta yaguna sannan tace "Shi yasa bana son zuwa gidan mutum yin ciniki sabo da bana son dogon ciniki karshe kuma na ɓata kafata a iska, to ni gaskiyar in da zan iya siyan katifar nan dubu 10 in yayi miki to duk sabon tar sa ai yazama na hanu, sannan kuma zaki bada kuɗin wan da zan nima ya kai min gida". Mama tace "Gaskiya katifar nan yafi haka kodun halin da nake ciki yaci kiduba lamarin kigani". tafiya dillaliya tasoma tana faɗin "To shi kenan kya iya nemo wata ta siya nidai daga kan dubu goma babu kari yo ribar nawa zanci ajikin sa". shiru Mama tayi tana juya lamarin cikin matukar damuwa da tashin hankali. taduba gabas ta duba yamma batada wata mafita,da yarage ta sai da mata haka bata da in da zata sami kuɗaɗen da ake nima a asibiti bata dasu bata da dalilin su, ganin tana kokarin fita a ɗakin da sauri tace "To ki bada hakan". Nan dillaliya ta caske dubu goma ta bata da fari tace zata cire naira ɗari uku acikin kuɗin ta bai wa ɗan dakon da zai kai mata katifar gida, Mama tace dan Allah tai maka kada ta cire ko sisi cikin kuɗin ta bita bashi zata bata... Kuɗin mama ta haɗa da wan da ta ciro a asusu yazamo dubu shashida da ɗari biyar, ɗakin ta bi da kallo babu wani abun da zata kuma ɗagawa ta siyar wan da zai bata ko da dubu 2 ne bare yacikita ragowar kuɗin,dama katifar ce kaɗai a cikin ɗakin sai ɗan tarkacen ta da ayan zu take ganin basu da amfani tun da bazata sai dasu su kawo mata kuɗi ba. numfashi ta sauke gaba ɗaya hankalin ta na asibiti da halin da HAMDAH take ciki, tasan tana can tana kan shan azaba. da sauri ta fita ta nufi gidan Malam Musa mai maganin maciji dan suna mutun ci dasu sosai a tsakar gida da sami Zainabu matar malam musa tana al'walan sarllar isha, bayan sun gaisa Zainabu ta ɗan yi dari tace "Mama mai awara kin biyo bashin awar ki na shekaran jiya ko? kin ga Wlh kwata-kwata na mance da naci bashin awara sai da na ganki na tuno". Mama tace "Wlh Ni ba abun da ya kawo ni ba kenan ai nima na mance da ma kin siyi awara, rancen kuɗi nazo kibani HAMDAH na asibiti za'a yi mata ai ki,kuɗin hanuna basu kai wan da ake nima a asibiti ba dan Allah ki ranta min bayan suna in sha Allahu zan biya ki". salati Zainabu ta saka tamike tsaye tana faɗin "Subhalallahi ayya HAMDAH yan da haihuwar yazo mata kenan Allah sarki yanzu an yi ai kinne?". Mama tace "A'a ni ake jira nakai kuɗin yanzu sai a mata". da sauri Zainabu ta shige ɗaki tana faɗin "Ikon Allah Allah yabamu da sauki". tafito rike da kuɗi ta mikawa mama tace "Wlh iyakacin arzikina kenan ɗaka da waje wannan dubu huɗun gashi malam yafita bare musa ran samun wani abu a gurin shi duk da dai shima naji yau yana kokawa". Mama ta amshi kuɗin tare da faɗin "Wlh hakan ma na gode zan haɗa dana hanuna na kai musu suyi mata ai kin kafin gobe na nemo musu cikon". tajuya da sauri tanufi kofa, Zainabu tabita da addu'a da fatan Allah yasa a yi ai kin a sa'a... Gida ta koma ta ɗauki laidar kayan jariri da take siya da ɗai-ɗai tana ajiye wa idan HAMDAH ta haihu za'asawa abun da ta haifa har na kwana bakwai,wato kala bakwai kenan kayane irin wan da mace da na miji zasu iya sawa,da ɗan sauran kayakin bukatu na jariri a talakance. tafito ta tari abun hawa tanufi asibitin. ko da ta isa ta kai musu kuɗin ta rokesu da Allah kan suyi mata ai kin idan Allah yakai rai gobe zata kawo musu ciko. Nan suke sanar mata ai ammayi mata CS ɗin sabo da ganin rayuwar ta da abun da ke cikin ta suna cikin haɗari. wasu nurse's ne guda biyu suka iso in da su Mama suke tsaye da ɗaya daga cikin Dr ɗin da sukayi wa HAMDAH CS, ɗaya daga cikin nurse ɗin tadubi mama tace "Tun ɗazu muketa nemanki Ina kayan babys da sauri mama tamika musu ledan dake hannunta su shige labour room domin su kimtsa babyn. Mama ta dubi Dr tace "Likita ya ita mai jegon dai?". Dr ta juya tashige room ɗin dake gefe da labour room tana faɗin "Babu komai in sha Allah har an fito da ita ma tana wannan room ɗin". wuf Mama tayi zatabi bayan ta tayi saurin cewa "A'a tsaya tukun akwai likitoci a kanta suna ai kin su bari su gama tukun". tafaɗa tana shigewa cikin room ɗin. ajiyar zuciya Mama ta sauke tanayiwa Allah godiya, taja gefe ta tsaya idanunta akan kofar da akace HAMDAH na ciki. Bayan wasu ƴan mintuna likitoci'n suka fito Mama na ganin da sauri ta matso in da suke tana tambayar su ya jikin nata, sukace zata iya shiga yanzu. cikin hanzari ta juyo zata shiga cikin room ɗin tajiyo Muryar nurse's ɗin da suka karɓi kayan jariri suna faɗin "Yauwa mun gama ga baby's ɗin". da sauri ta juyo da mamaki take kallon nurse's ɗin dukan su rike da baby, sai tasa hannu takarbi guda daya na hannun wacce take kusa da ita tajuya zata wuce, sai ɗayan nurse din tace "Baki da me taimaka miki ne ga ɗayan fa, ko kin bar min ne". tafaɗa tana murmushi ɗayar tace "Ai kuwa nima yaran sun tafi da ni Wlh ni ban taɓa gyara kyawawan baby twin's irin waɗan nan ba kallesu fa wlh ko ƴaƴan turawa bazasu nuna musu komai ba kai ni sai nagama sunfi min ƴaƴan turawan". da maki Mama ke kallon su da jin abun da suke faɗa tace "Kuna nufin yanbiyu ne ta haifa duka waɗan nan ƴaƴan ta ne?". tayi maganar cikin matukar mamaki. dariya sukayi mata ganin yanda take maganar bilhakki, Nurse ɗin ta mika mata ɗaya babyn tana faɗin "Duk natane,yauwa na mijin shi aka fara cirowa kafin macen". rungumar yaran mama tayi a kowani hannunta guda tajuya cikin tsananin farin ciki har da kwalla tanafadin "Alhamdullilahi Allah mun gode maka". cikin hanzari tashige dakin da aka kai HAMDAH. dasauri takarasa inda take kwance da yaran a hannunta tana fadin "HAMDAH bude idon ki kiga abin da kika haifa". jin Muryar mama yasani buɗe idanuna a hankali, asannu nashiga juya kai na saiji nayi kamar an ɗaɗɗaure ni, dasauri mama tamatso kusada ni ta ajiye yaran dake rike a hannunta a gefe na,tana cigaba da faɗin "Allah mai iko kai sannu HAMDAH sannu kinji". asannu najuyo kaina da kyar kallon yaran da mama ta ajiye a gefe na nayi kana daƙyar nabude baki murya can kasa nace "Mama waƴannan yaranfa?". sai da ta maso sosai kafin ta iya jin abun da nake faɗa, fuska ɗauke da yelwataccen murmushi tace "Dukkansu nakine". cikin tsananin farin ciki da murna Mama ta ɗago ɗaya daga cikin yaran ta karkato shi saitin fuskanta tana faɗin "Kalli kyakkyawar mai gidan nan nawa da sukayi ta baki wuya,ga kawata ma nan". ido na kurawa jaririn yayin da naji wani irin mummunar faɗuwan gaba ya ziyarci zuciyata, fuskar Ya SALEEM kaɗai nake hangowa kan fuskar jaririn, idanuna na rumtse da karfi tare da kuma buɗe shi kan fuskar jaririn, mai mugun kama da Ya SALEEM tamkar an tsaga kara. Mama ta mai da yaron ta kwantar ta ɗago ɗayar tana faɗin "Ga kawata nan tabar kallah masha Allah". hancin babyn ta lakata tana washe baki da cigaba da faɗin "Ikon Allah wannan girman ciki yayi yawa ashe dai kune kuka baje ciki". kai na na rausayar gefe da kyar, jin wasu zafafan hawaye sun zubo min kokarin danne zuciya ta daketa son fama min mikin dake cikin ta nake, rumtse idanuna da karfi nayi duk yan da naso danne zuciya ta sai da na tuno. fahimtar yanayin da na shiga yasa Mama tayi ta jana da hira duk da bana ammsa mata da ido kawai nake binta. haka tayita kokarin gusar min da damuwar da take hangoshi cikin idona, har sai da taga na saki raina, har naɗan juyo da kaina ina kallon yaran, Allah mai girma da ɗauka wai duk waɗan nan ƴaƴan a cikina a ka ciro su. Mommyn twins ce Ranan Azaune mama ta kwana rike kuma da yaran idan ɗaya yayi motsi sai ta aje na hannunta taɗau ki ɗayan, duk san da na farka sai na ganta zaune tausayin ta yakama ni, na tabbata tun da rana dana fara labour batasa komai a bakinta ba har kuma yanzu, domin gabakinta abushe, haka tayi-tayi dayaran har gari yawaye. washegari da safe Zainabu suka zo da ita da wata makociyar Mama,sukazo mana da abun karyawa niki-niki. suna rike da yaran a hannunsu kowa sai sanbar ka yake, Zaunabu data kurawa ƴa macen ido tace "Oh ikon Allah jibi waɗan nan yara wazai gansu yace tagwaye yara katin-katin dasu kamar haihuwar ɗaya, kai sannu HAMDAH gaskiya kinyi kokari waɗan nan kam ai sai dai CS ɗin". murmushi matar da sukazo da ita tayi tace "Wlh kam yara tabar kallah ga wayo ni dai tun zuwan mu idanun su abuɗe suke". Mama tayi dariya tana faɗin "Waɗan nan awaye kazan birni ai tun jiya idanunsu a buɗe yake suna jin motsi zasu juya ido gun kamar masu jin magana, kunga wannan bakyauyiyar kawar tawa idanunta a kan fanka, shi ko angon ido yakurawa kwan wuta". dariya duk suka saka ai kuwa sai yaran suka shiga raba ido kamar sun san me ake faɗa, Zainabu tace "Ai kuwa yaran akwai wayo ga yan da suke kokarin juya kai suna jin magana"... Haka suka yi ta kallon yaran cikin ban sha'awa. nan mukata hira dasu sai kusan azahar sukatafi. mama ta rakasu tadawo tana dawowa daga rakiyarsu nadubeta cikin yanayin gajiya da kwanciyar da tun jiya ban motsa daga in da aka kwantar da ni ba, nace "Mama dan Allah ki dagani nikam nagaji kokuma injuya gefe". Mama tace "Sunce bayanzu ba". dasaura nace "To Mama kishin ruwa nakeji dan Allah kibani ruwa nasha". dubana take cikin tausayawa da tsigar rarrashi tace "Kiyi hakuri HAMDAH su sun fimu sanin dalilin da yasa suka ce kada a baki komai tun da ai kin sune ki kara hakuri dan Allah kibari likitocin suzo tukun". kai kawai najuya cikin gajiya da kwanciyar guri daya gamugun ƙishin ruwan da nakeji... karfe huɗu na yamma har lokacin ina nan kwance duk yadda naso Mama ta ɗagani ko taban ruwa nasha fir taki. kuka nasaka mata ina faɗin "Ni dai nagaji nagaji ƙishin ruwa nake ji". Ido Mama ta zuba min tana jijjiga baby boy ɗin dake ta zandara ihu tun ɗazu,ta bashi ruwa yafi a kirga da zaran ta cire fida a bakin sa sai ya sa kuka. Ana cikin haka sai ga ɗaya daga cikin Doctors ɗin da sukayi min CS yashigo, yace "Mama mai kikayi wa pationt din mu ne haka take kuka". yafaɗa da murmushi yana karaso wa bakin gadon da nake, Mama tace "Wallahi tuntini wai so take a ɗaga ta tagaji kuma wai kishin ruwa take ji shine nace tayi haƙuri sai kunzo". murmushi Dr yakuma cikin kwarewa da iya tafiyar da mara lafiya ya dube ni yace "Idan zaki iya tashi to tashi". nayi yunƙurin tashi naji Nakasa sai ji nayi kamar cikina yana buɗewa in da aka min CS ɗin, ido na matse sai ga hawaye sharr. Ido yaɗan kura min kana yace "Sorry bari nurse's suzo su tai maka miki". yafita ba jimawa nurse suka shigo suka ɗagani suka goge min jiki suka kimtsa ni, kana suka cewa mama takawo ruwan zafi kadan a kofi akabani nasha, sannan sukace na gwada kwanciya da kai na in zan iya,nan ma na kasa,su suka mai dani suka kwantar dani. sukace wa mama taringa haɗa min milo inasha duk bayan awa daya domin zai taimaka min yakawo min ƙarfi ajikina. tace to insha'allahu nan suka fita... Da daddare nurse's ɗin suka kuma zuwa, yanzu kam cewa sukayi na tashi da kai na daƙyar na iya mikewa zaune, bayan sun gama gyara min jikina sukace na kwanta da gefe in zan iya shima nakwanta, Washegari ma da kaina na tashi nurse's suka gama ai kin su suka fita, Mama tasa min pillow a baya na na jingina dashi, bayan nagama shan tea mai zallar milo da Mama ta haɗa min, tadube Ni tana faɗin "To tun da kin koshi kibashi nono yanzu kam kin ga dai tun jiya kuka yake, ga ƴar'uwar sa ma yau ta tashi da kukan, yunwa duk suke ji". Baki na tura dan tun jiya take ta bina nabashi nono toma ni ta'ina ma zan fara, miko shi tayi taɗaura shi kan cinya ta sai dai bata sake shiba tana rike dashi ta ɗan gyara shi ta inda bazai fama min ciwo ba, tace "To ɗan gyara sai ki bashi"... yana kama nonon nayi saurin fizge nonon a bakin sa tare da sakin ƴar karamar kara, na yarfe hannu ina faɗin "Wayyo zafi". ai ko shima sai ya saki kuka yana cusa hannunsa cikin baki, Mama tace "Daure ki bashi kinji". sai da Mama tayi ta lallaɓi na kafin na yarna na maida masa nonon bakin sa ina matse ido harda kwalla. bayan yasha ta kwantar da shi ta ɗauko ta ita ma tasha. kana tayi musu wanka nan da nan kuwa sukayi bacci....★ Kwanan mu uku a asibiti kullum sai Zainabu ta ai ko mana da abinci. zuwa yanzu kam jikina Alhmdllh dan har ina sauka na taka da kaina, Muna zaune Mama nata jana da hira yayin da take ta yiwa yaran wasa. Malam musa yashigo da sallama bayan an gaisa yake tambaya haryanzu baban yaran baisamu isowa bane? Mama tace "Eh. a takai ce. ƙasa nayi da kai na ina wasa da yatsun hannuna yayin danaji wani abu yataso yatokare zuciyata nan take naji ƙwalla yaciko min ido dasauri namai dasu,ta hanyar ambaton sunan Allah a cikin zuciya ta, Har yanzu mutanen da suke hulɗa da Mama basusan ko wacece niba, har yau Mama bata sanar musu koni wacece ba abun da kaɗai suka sani takuma sanar musu Ni ɗiyar kanin tane kuma mijina soja ne yana bakin ai ki haihuwa nazo, rumtse idanuna nayi yayin da kwallar da naketa mai dasu suka zubo, nakai hannuna nashare batare da nabari sun gani ba. Malam Musa yace "Ayya to Allah yataimaka yaune kwanan su uku ko? yakamata a musu huɗuba gashi kuma har yanzu bai samu isowa ba". da sauri Mama tace "Haka ne kuma inaga zuwan sa kam ma zai kai har bayan suna ai ko baza'a jira har sai yazo ba za'a yi musu huɗu ba, Malam ayi musu huɗu ba kawai, yoo yaushe za'a zauna zaman jiran sa". Malam musa yace "To babu damuwa, shin yafaɗi sunan daza a sa ma yaranne?". mama tace "Eh". takalleni tare da faɗin "Yayama sunan daya faɗa miki?". shiru nayi kaina a kasa, sai da mama ta kuma mai-maita tan bayar kana nace "Idris da Aysha" tabbas babu sunan da ya dace da yaran face sunan Abbu da Inna, sun nuna min so da kauna da kuma gata. bakuma zan taɓa mancewa da su a rayuwa taba. Malam Musa yace "Masha Allah yara zasuci manyan suna". gyara rukon baby boy din dake hannusa yayi kana yazura hannunsa cikin aljuhu yaciro dabino, Nan yayi Masa huɗuba da suna Idris kamar yadda addini yakoyar, kana ya mikawa Mama shi yace "Allah yaraya Idris bisa Sunnah". Mama tace "Amin". ta kwantar da shi ta dauko baby girl din ta Mika masa Nan ita ma yayi mata huɗuba, kana yamikawa Mama tare da fadin "Allah yaraya Aysha". Mama takuma amsawa da Amin Amin,tare da masa godiya. Nan yayi Mana sallama yatafi..... Mama ta dubeni da murmushi dason gusar min da damuwar da take hangoshi kan fuska ta, ta kalli yaran tana faɗin "Masha Allah kinwa Inna takwara ne ko wa kanki?". ta faɗa tana murmushi, ido na tsurawa babyn kana nace "Wa Inna nayiwa takwara kamar yadda nima naci sunan ta". dariya Mama tayi tare da lakata hancin babyn tana faɗin "Kaga Aysha ɗiyar Aysha kakar Aysha uban giji yaraya ku da imani, to me za'a rika kiran su yanzu kuma?". tafaɗa tana duba na fuska ɗauke da murmushi. shiru naɗan yi alamar nazari zuwa can nace " *NASEEM DA NASMAH*" baki Mama ta washe tana faɗin "Iye Ah gaskiya sunan yayi kama dasu". yanzu kam sai da mama tasani murmushi idanuna a kan yaran ina duba kamar da tace sunan yayi da su....★ Yau Zainabu da kanta takawo mana abincin dare da kuɗi naira dubu 5. nan take cewa Mama malam Musa ne yabata rance, ranar da tazo niman kuɗine tayi wa malam ɗin magana ko yana dashi, yace Wlh baya dashi sai yau ya samu shine yabata takawo. Mama tayi ta mata godiya tace dan Allah tayi masa godiya kuma in sha Allahu zata biya da hannunta da yar dar Allah. Nan da nan kuwa takai ragowar kuɗin da ake binsu a asibitin. Washegari da safe aka sallame mu.... ranar da muka dawo gida a ranar mama tafara awara,na tausaya mata kwarai, ranar sai da nayi kuka dan nasan dan ni ta fara sana'ar a yau wan da yakama ta ace hutawa take da ɗawai niyar asibitin da ko baccin kirki batayi, sai gashi muna shiga gida tasoma wani ai kin... ana gobe suna da yamma bayan Mama tayi wa yaran wanka muna zaune ina cin abinci, Mama na goye da Nasmah yayin da Naseem ke rike a hannunta tanata jijjiga shi, Mama ta dube ni tace "Wannan mai gidan fa in baiji motsi a bakin sa ba baya gane wa". fuska na kwaɓe nace "Mama yanzu fa suka sha". "To yaro shi ina ruwan sa ciki kawai yasa ni gama dai kiba shi yasha, ga kawata ma na kan motsi". Kamar na kurma ihu haka naji, yanzu suka sha babu jimawa gashi yanzu wai suna nima, cikin tura baki nace "Allah kaɗan zan basu anjima kuma abasu kunu". Mama tace "Kunu kuma?". nace "Eh". dariya tayi tace "To shike nan yanzu dai ki basu susha"....... Washegari yakama ranar suna, da sassafe Mama tayi min wanka kana tayiwa Nasmah da Naseem, nashirya cikin doguwar riga ɗaya daga cikin kayana da nazo dashi tun wancan lokacin yaɗan kasa min sabo da ciki sai na ajeshi bana sa shi, shi yana nan har yanzu da ɗan sabon tar sa. ɗan ribar awara da tasamu na kwana biyu da shi tayi cefane ta siyi shin kafa ta haɗa da sauran waken kosai suka girka abinci da Zainabu da tun da safe tazo. da rana makota suka shishshigo, Mama mai yin biki ne tana da kokarin shiga wa mutane biki, duk wan da take yin biki da su kowa sai da ya kawo mata rigar baby wasu na maza wasu na mata da omo da sabulu har da man shafa wa. Naseem yasamu kaya kala huɗu yayin da Nasmah ma tasamu kala huɗu. da yamma kowa ya watse.... Bayan suna Mama tafara niman kuɗi ba kama hannun yaro domin biyan bashin da ake binta, ba iya sana'ar awara da kosai kaɗai ta tsaya ba har da kayan miya tana sara tana siyar wa, da duk wani abu na nasa'ar cikin gida da tasan zata sami riba a kansa tana siya ta siyar. cikin yar dar Allah da ikon sa yadafa mata duk abun da zata taɓa na sana'a sai ta sami riba a kansa... ranar da muka yi arba'in ranar ta kai wa Zainabu da malam Musa kuɗin su,kamar yan da tayi musu alkawarin bayan suna zata biya su takuma jajirce wajen nima har ta samu, tayi ta musu godiya..... Tun daga ranar hankalin ta ya kwanta ta kuma mai da hankalin ta wajen kula da Ni da kuma ƴaƴana, duk wani ribar da zata samu a kanmu yake kare wa. yanzu nawar ke garau idan ka ganni bazaka ce CS aka min ba, nakan ji mutane da dama suna cewa jikina mai kyau ne bana da kan jiki..... Haka mukayi ta lallaɓa rayuwa nakuma daure da juriyar shayar da yaran,sai dai na rame kwarai suko kamar hurasu ake, sunata girma da kuma kara wayo sosai, lokacin da suka cika wata uku, Mama ta haɗa musu garin kunu na alkama waken suya da gyaɗa, nan ne naɗan sami sauki, da shi muka cigaba da rainon su... Ranar wata asabar..........!★ Mommyn twins ce Ranar wata asabar hakan yayi dai-dai da watan su Naseem huɗu da sati biyu, Zaune muke a tsakar gida, ina rike da Naseem a sakiyar kafafuna dan alokacin suke koyon zama. Mama na goye da Nasmah tana bacci, ita kuma tana ta ɗan aikace-aikacen ta. Sallama mukaji daga bakin kofa da karfi, ba Mama kaɗai ba hatta ni sai da naji wani irin muguwar faɗuwar gaba dajin muryar mai sallamar, yau kusan sati ɗaya kenan Alhaji Mamman sai yayi sallama a gidan kullum sai yazo maganar kuɗin hayar sa, wan da yanzu ya ninku yazama na shekara biyu da rabi. takuma sana diyyar mune hakan ya faru kula da Ni da ƴaƴana shi ya hana ta ajewa Alhaji Mamman kuɗin hayar sa, yunkurin mikewa nashiga yi jin yacigaba da kwaɗa sallamar ba ko kakkautawa, kafin na mike ma ya sako kansa cikin gidan yashigo, yana faɗin "Fasuma kinsan dai ba gidan mijin ki bane ba,kuma bamu haɗa kuɗi da ni da shi mun siya ba, sannan kuma koda ace ma mun haɗa kuɗi da ni da shi mun siya, kinsan dai yanzu yariga da ya mutu kuma dole a cire min nawa a ciki, bare kuma gida gida nane ba nashi ba ko bulo ɗaya bai ɗaura a kan gidan nan ba, bare ki zauna kice kina cin gadon sa, dan haka kifita min a gida yau babu afuwa babu rangwami, kifita min a gida yau zan saka ƴan haya acikin gida na, gasu nan ma munzo tare da su, ina bukatan kuɗi dan sabo da kuɗi na tara kafin na gina gidan, ga ƴan haya nan mun iso da su ga kayan su can a moto dan haka ki fita kibasu ɗaki." yakaraso ciki yana muzurai tare da cigaba da faɗin "Ganan masu shiga gida sun iso ke kaɗai suke jira kifita kibasu ɗaki, dan yanzu ɗakunan gida nasune su sun iya biyan kuɗin haka, sannan kuma bawai na bar miki kuɗin haya da na ke binki na shekara biyu da rabi bane ba, ina binki bashin su kuma zaki nimo kibiya ni kaya na babu rangwami acikin watannan zaki biya ni in baki bada ta daɗi ba zaki biya a hannun hukuma." Cikin tsananin tashin hankali mara misaltuwa na ɗago Naseem dake hannuna na goya shi, na mike tsaye yayin da Mama tarika haɗe hannayen ta biyu cikin matukar tashin hankali tace "Dan Allah Yaya kayi hakuri insha'allahu ina nan ina kan tara maka kuɗin nan kayi hakuri dan Allah kasan dai yanzu abubuwan sai a hankali,dan Allah kayi hakuri in sha'Allah zan haɗa maka kuɗin acikin ƴan kwana kin nan, kakara yimin afuwa". cikin ɗaga murya Alhaji Mamman yace "Dakata dan Allah Ni kin ishe ni kullum ke kenan maganar ki ayi miki afuwa ayi miki rangwami, wai shin kan kuɗin nan in da rangwami da afuwa ake tarashi zai taru ne, in dai da akwai rangwami acikin tara dukiya da zai taru ne? nifa kuɗi kawai nake bukata, shi kuma nake son tarawa, kin san ta yan da akayi na tara kuɗi na siyi gidan?, nifa kuɗi kawai nake bukata, in da ace kin fita tuntini a gidan nan da na tabbata na tara kuɗin da yafi abin da ake tunani dan haka ni kifita min agida kawai babu wani rangwami." fuskarsa yajuya ta bakin kofa ya ɗaga murya yana faɗin "Kushigo da kayan Bismillah ga gidan kushigo da su". kofar da yake kallon na zubawa ido in da naga shima ya fuskanta yana maganar, wasu mata da ƴan matasa ne suka fara shigo wa da kaya, suka ta shigowa da shi suna ajiye wa... Hannu mama ta kuma haɗawa tana cigaba da rokon sa da haɗa sa da Allah da yi masa magiyar in sha Allahu zata biya sa kuɗin a cikin watannan, yace "Dai na haɗa ni da Allah ki cuce ni, na dai faɗa miki babu bulo ɗaya da mijin ki ya ɗaura kan ginin gidan nan, nariga da na gama magana yanzu bani da hannu acikin wannan gidan na nariga da na bada hayan shi,na karɓi kuɗin sa dan haka fita ki basu gida yanzu nasu ne". yajuya yaso ma tafiya yana cigaba da faɗin "Kuɗi na da nake bin ki bawai na bar miki bane kuɗina yana nan a kanki kuma zaki biya ni, na baki sati biyu ki biyani kuɗi na idan ba haka ba sai nayi miki rashin Mutun cin da baki tunani, kin san ni a kan kuɗi ko uban waye ma zan iya masa rashin mutunci ko shi mijin naki da muke uba ɗaya bai isa yaci kuɗi na ba tun da bashi ya nemo min ba." yayi waje yana cigaba da zazzage bala'i. Bayan sa Mama tabi tana cigaba da haɗa shi da Allah har kofar gida ta bishi,shi ko yaja garen sa yahaye babur ɗin sa yayi gaba. suko mutanen da yazo da su sai shigo wa da kaya suke suna jibgeshi a tsakar gida, tuni hawaye yafara sauka a ido na, muna tsaye cirko-cirko har suka gama shigo da kayan. matan suka dubi Mama sukace "To mun gama shigo da kaya yazu shirya shi cikin ɗaki ga gurin yafara rufa wa kar ruwa ya sauko ya jika mana kaya." da sauri Mama ta dubi matar batare da tace komai ba, Hannuna Mama tarike tana faɗin "Zo mu fitar da kayan". cikin zubda kwalla nace "Mama idan muka fitar da kayan ina zamu kai?". tace "Allah bazai hanamu in da zamu kai ba." Haka mukayi ta fito da kayan mu nuna kai shi can waje kofar gida, tas muka fito da kayan muka jibgeshi waje duk da dama bawani kayan kirki bane. muna tsaye a kofar gidan Zainabu ta iso mu hankali tashe tana faɗin "Mama mai awara yanzun nan yaro yazo yace min yaga kuna ta fitar da kaya, wasu kuma suna shigar wa ciki, Mama da ma tashi zakiyi shine baki faɗa mana ba?." Murmushin yake mama tayi kana tace "A'a mai gidan ne yazuba ƴan haya aciki shiyasa muke tashi muma tashin yanzu ne yasa memu bawai tuntini da ma da shi bane". Ido Zainabu ta waro tare da buga kirji tace "Ya zuba ƴan haya a cikin gidan bayan da wasu masu hayan aciki, ban taɓa ganin haka ba, ba'a taɓa ɗaga ɗan haya rana a saka batare da an bashi lokaci ba sai an bashi kwanaki ya kama gidan da zai zauna kafin a ɗaga shi, ba irin wannan ɗagawar babu sanar wa ba, to yanzu ina zakuje Mama kuna da wani gidan da kuka kama ne?". Mama tace "Ko ɗaya yanzu dai zamu ni mi wani gidan hayan da zamu zauna". "Gaskiya kam amma wallahi bai kyauta ba ai ba haka ake yi ba ba'a taɓa ɗaga mai zaman haya haka lokaci guda ba, sai dai a baka lokaci ka kama wani gidan hayan sai ka tashi ba irin haka lokaci guda ba". Mama kam murmushin karfin hali yacigaba da yi, Niko hawaye ne kaɗai ke zuba a ido na naka iya furta komai. Zanabu tace "Mama ku tattaro kayan kizo muje ga guri yafara rufawa hadari yana kan taso wa". ta sun kuya tana tattaro kayan tare da cigaba da faɗin "Kuyi sauri kada ruwa yasau, ko kuzo muje kutara su a zauren gidan mu kafin ku sami wani gidan". Mama tace "To Zainabu". nan muka shiga kwashe kayan muna kaiwa gidan Zainabu a zauren gidan ta muka tara kayan gaba ɗaya sannan muka shige ɗakin ta dan lokacin tuni ruwa ya sauko... Tun da aka fara ruwan nan bai tsaya ba har yamma, har Malam Musa yadawo yazo yasa memu a gidan, koda yaji labarin bai ji daɗi ba kwarai yace Alhaji Mamman bai kyau ta ba bahaka ake yi ba,sai dai yasan waye Alhaji Mamman karamin ai kin sa ne yin hakan. Yacewa Mama bari a ɗauke ruwa zai fita yake yataya ta niman gida ko Allah zai sa a samu a yammacin,. Mama tace ita ma ɗin ruwan take jira yaɗau ke tafita niman gida. Gidan malam Musa ɗaki ɗaya ne tak a gidan shine kuma wan da suke zaune da matar sa a ciki. dan haka zaure yako ma yaje ya zauna yabar mu acikin ɗakin, gaba ki ɗaya Mama a takuri take ganin mai gidan yako ma zaure ya bar mana ɗakin. wasa-wasa ruwan nan bai ɗauke ba sai daf magriba, dan haka Malam Musa yace Abar niman gidan sai gobe tun da yanzu dare yariga da yayi, a zaure yakwana yabar mana ɗakin... Washegari da sassafe Mama tafita neman gidan da zamu koma bata dawo ba sai wajen azahar, tadawo gaba ɗaya a galabaice, a ɓangaren Malam Musa shima bai jima da dawowa daga niman gidan ba, Muna zaune a ɗaki Zainabu ke tambayar Mama Allah yasa anyi sa a an sami gidan. numfashi mama ta sauke cike da ɗinbin damuwa tace "Wallahi nagama iya yawo na ban sami gida dai-dai da kuɗin hannuna ba duk gidan da naje niman hayar sa gaba ɗaya sun fi karfin kuɗin hannuna, azaman yanzu kuma gaskiya masu rangwami sunyi karan ci". kai Zainabu ta girgiza cike da tausayawa kana tace "Gaskiya kam yanzu rayuwa tayi tsada Allah yayi mana magani". Amin muka amsa dashi, gaba ki ɗaya jikina yagama yin sanyi. Mama ta mike ta nufi zaure in da kayan mu yake can,ganin ta ɓata lokaci bata dawo ba sai na mike na bi bayan ta, ganin ta nayi tana shirya kaya cikin ɗan kari min jaka gaba ki ɗaya hankalin ta a tashe, ta dube ni tare da faɗin "Zanje garin mu HAMDAH kamar dai yan da na taɓa baki labari ni ƴar Yola ne aure ne ya kawo ni nan, yanzu rabona da Yola shekara 7 kenan zanje ni na dawo in sha Allahu kwana biyu zanyi na dawo, zan tafi mana da wasu kayayyakin mu zanje na duba kalar yanayin zaman can idan naje nasa mu matsuguni,duk da dai dama muna da gidan gado kamar yadda na taɓa baki labari yanzu dai zanje na duba acikin gidan gadon mu idan akwai ɗakin da zamu zauna, zan dawo nazo na ɗau keki mukoma, kwana biyu kacal zanyi na dawo sai na ɗauke ki mu koma tare". ta ciro kuɗi naira dubu biyu da ɗari biyar ta mika min tace "Ga wannan ki rike a gurin ki ko zaki bukaci wani abun, kin ga suma nan basu da karfin da zasu iya ɗawai niyar ku duka duk da bawai jimawa zanyi ba kwana biyu ne ka cal, Amma ki rike zai iya yi muku amfani,ko zaki ga abun da kike so ko su Naseem da Nasmah sai ki siya musu". numfashi na sauke jiki a sanyaye dan Mama ta taɓa bani labarin family'n su Su biyu ne agun mahaifin su ita da wanta na miji, lokacin auren ta yayan ta baiso auren da wan da take so ba dan lokacin mahaifinsu ya rasu a haka dai akayi auren sam baya so, shi yasa ko taje gidan ma bata jin daɗi shi yasa takan daɗe bataje gidan ba dan ko taje ma baya sauraran ta, ko da mijin ta yarasu taje amma yaki yabata fuska tazau na agidan, sai dai ta alakan ta hakan dan gidan nasa ne yanzu sabo da shi yaci gadon gidan, abun tun yaranta har yanzu tana ta kan fama, har yakai ga yanzu shi yayan nata yarasu sai dai matar sa ta ari abun ta yafawa kanta, ta kanainaye gidan tace gida natane da ƴaƴan ta dan haka babu wan da ya isa ya zauna mata a gida. dan a lokacin da mahaifin su Mama ya rasu yayan ta shi aka basa gadon gidan in da ita aka bata gadon gonar mahaifin su... idan taje gidan matar tarika mata wulakanci da gani-gani shi yasa ma shekaran ta 7 bataje ba... Hawayen fuskata na share kana nace "To mama sai kin dawo Allah ya kiyaye hanya amma Mama ki dawo da wuri dan Allah". tace "Insha'allahu zan dawo da wuri HAMDAH kwana biyu zanyi da yar dar Allah zanje naga yanayin zaman gurin in yaso ma zan saida gonana da yake can sai na dawo na kama mana gida a nan ko kuma na kama mana a can Yola sai na dawo na ɗauke ku sai mu koma". nace "To Mama Allah ya kai mu ya kiyaye miki hanya" ta amsa da Amin Amin. Da azahar ɗin muka fita yi wa mama rakiya ni da Zainabu har bakin hanya muka kai ta yayin da take rike da Nasmah, da tun dawowar ta daga niman gida ƴar ta nanne mata sai da ta goye ta, sai da muka tari mai abun hawa kafin ta miko min ita, kana ta karɓi Naseem tana yi masa wasa shi ko sai wage mata baki yake, duk yaran sai dariya suke mata itako sai wasa take musu,har sai da mai abun hawa yayi magana kana ta miko min Naseem, kuka ya saka yana zillo alamun zaije gurin ta, murmushi tayi tare da lakata kuma tun sa tace "Mai gidan ka zauna zanje nadawo yanzu bazan daɗe ba zanje na nimo sadaki na kawo maka". dariya ya saka kamar wan da yasan me aka ce, Zainabu tace "Ai kam kine mo da yawa dan yanzu mata suke bawa maza sadaki". Mama tace "Ai kam". kana ta shige abun hawa muna ɗagawa juna hannu yayin da hawaye ke zuba a ido na, muka juya muka koma gida...!★ Mommyn Twins ce Ranar a zauren malam Musa yakuma kwana ya bar mana ɗakin, washegari haka na wuni sukuku bani kaɗai ba hatta Naseem da Nasmah idan ka kallesu kasan sunyi kewar Mama,duk da kuwa Zainabu tana jan su ajiki tana yi musu wasa, Malam Musa kuwa yana iya bakin kokarin sa ya kawo mana abinci sosai Zainabu ta girka mana.... yau kwana biyu kenan da tafiyar mama inata murna da zuba idon ganin dawowar ta dan nasan yanzu kam tana hanya, ganin bakina yakasa rufuwa Zainabu tayi ta zolaya ta tana yi min dariya. murmushi nayi nace "Ai in sha Allahu yau zata dawo". Ido nayita kurawa hanya dan ganin isowar Mama har yamma shiru babu wani labari, wasa-wasa har dare yayi zuwa lokacin kam shiru na zauna cikin damuwa jikina yagama mutuwa. har dare yayi nisa sosai nan ne na cire raina da dawowar mama a yau na sa a raina wata kila sai gobe zata dawo. goben ma haka shiru yanzu kam hankali na yakai kololuwa wajen tashi, ba abun da ke damuna kaɗai ba kenan, duba da gidan da nake zaune duk da Ni basa nuna min wani hali ko kaɗan, Amma bana jin daɗi badun komai ba, sabo da ganin shi mai gidan da gidan sa a zaune yake kwana gashi yanzu yanayin damina kusan kullum sai anyi ruwa ga sanyi haka akan taburma take kwana acikin zauren. gaba ɗa hankali ya ninku wajen tashi, ace mai gida da gidan sa a zaure yake kwana zauren ma kan taburma ga sanyi. Yau kwanan mama biyar da tafi babu alamar ta. da safe na nufi zaure in da kayan mu yake naɗauki akwati na da nazo da shi tuntini na haɗa kayana kala biyar wan da tuntini da ma da su nazo naketa sawa har yanzu sun gama tsufa sun koɗe wasu ma har sun yayyaye sai da aka bisu da ɗin ki, na haɗa kayan cikin akwati, na ɗau ki kayan Naseem da Nasmah wan da suka samu a suna kala hurhuɗu sai kuma wan da Mama tasiya tun kan na haihu na haɗa su cikin akwatin, da ɗan sauran kayan bukata, nayi musu wanka nima nayi, Zainabu tazuba min ido ganin inata shiri kana tace "Naga kina ta shiri da haɗa kaya wai ina zaki ne haka da kaya?". nayi murmushi tare da duban ta nace "Zan bi Mama ne dan har yanzu gashi bata dawo ba". Zainabu tace "To ke da zaki jirata batace kijirata ba". nakuma murmushi tare da faɗin "Eh tace na jira ta amma har yanzu bata dawo ba kawai zan bita can ɗin". shiru Zainabu tayi kana tace "To shi kenan amma Ni inaga da kin daɗa kara hakuri ki jirata". nace "A'a zan bita kawai". tace to shike nan. Bayan nagama kimsa yaran na ɗauki Nasmah na goya na saka hijabi na kuɗin da mama ta tani na ciro sannan na ɗauki Naseem a hannu, Zainabu ta roko min akwati na har bakin hanya ta raka ni, na hau abun hawa zuwa tasha ina isa Na shiga motar YOLA........ Acan cikin garin Bauchi'n Yakubu kuwa zaune Ummi take akan sallaya..........!★ Kuyi hakuri dan Allah wlh sabar sauri ko editing ban yi ba😫 Mommyn twins ce Wani sassanyan kuka Ummi ta sake dai-dai lokacin da ta sallamar da sallar nafilar da take, ta ɗaga hannayen ta biyu tana kwararo addu'a yayin da hawaye ke sauka a idon ta, tun ranar da HAMDAH tasa kafa ta fita agidan kullum Ummi acikin kuka take. badare barana ko da yaushe acikin yimata addu'a take tana nina mata kariyar Allah a duk inda take. Wani sassanyar kuka mai matukar taɓa zuciya Ummi takuma sakewa lokacin da take jaddada rokon ta ga mahaliccin mu. yayin da muryar ta ke fita haɗe da sautin kuka. Fauzan da yanzu shigo War sa cikin ɗakin da sauri ya isa in da take yadurkusa gaban ta tare da kifa fuskar sa kan cinyar ta,sai ya saki kuka yana faɗin "Ummi dan Allah ki daina kuka Ummi kullum sai kinyi kuka Ummi ki dai na kuka". yafaɗa cikin matukar damuwa da ganin halin da mahaiyar tasa kullum take ciki, kansa ta shafa da hannunta ɗaya yayin da ta ɗago hannunta guda tashiga share hawayen fuskar ta. a hankali tace "Taso Fauzan yi shiru na dai na kukan". tafaɗa cikin sansanin karfin hali da son danne zuciyar ta da ke wani irin muguwar bugawa, Aduk san da ta nuna da HAMDAH irin yanayin da take shiga kenan sai dai na yau ya ninka na ko yaushe. yau bugun zuciya ne mai haɗe da ɗinbin tsoro. da sauri ta kai hannunta ta dafe kirjin ta tare da furta "Innalillahiwa'inna'ilaihirraji'un". da karfi cikin tsananin jin tsoron da ya lulluɓe ta.. cikin rawar murya mai haɗe da tsoro tacigaba da faɗin "Ya Allah ka kare baiwar ka aduk in da take a duk halin da take ciki,ya Allah kafini sanin inda take kakare ta da kariyar ka." Kuka sosai Ummi tafashe dashi ta rungume Fauzan da shima yakara sau tin kukan sa, kuka sosai Ummi take tamkar karamar yarin ya kuka. cikin Muryar kuka Fauzan yake cewa "Ummi kin ce Aunty HAMDAH zata dawo kullum haka kike faɗa gashi har yanzu bata dawo ba,Ummi yaushe Aunty HAMDAH zata dawo?". hawayen fuskarta tashi ga share wa yayin da take kokarin sai da hawayen da kuma kukan tace "Ko bata dawo ba Allah zai kare ta a duk inda take a duk halin da take ciki, shine mai kariya buwayar sa ya isa ko ina". taɗago Fauzan tashare masa hawayen fuskarsa kana taci gaba da faɗin "Yi shiru kaji a duk inda take tana cikin kariyar uban giji"..... Tun da muka fara tafiya nakejin wani irin yanayi a jikina, sai dai na kasa fassara kalar yanayin da nake jin kaina ciki, ina dai zaune cikin matar shiru yayin da Nasmah ke goye a bayana har lokacin Naseem kuma na rike a hannuna, duk kanin su bacci suke, daɗa gara rukon Naseem nayi kana na zuba wa titi ido. sosai motar ke sharara gudu kan hanya sai dai nayi mamakin ganin tulin tafiyar da mukayi mai nisar gaske wai har lokacin bamu iso garin Yola ba, tashin tun sassafe gamuna har bayan azahar a kan hanya duk da kuwa gudun da motar take. tun fasinjojin da ke cikin motar suna hira har kowa yayi tsit sabo da nisar tafiyar. karfe uku da rabi dai-dai muka isa wani gari in da direba yagyara fakin a gefen titi, numfashi na sauke tare da yiwa Allah godiya a raina nake faɗin "Kai wannan gari akwai nisa har sai yanzu muka iso gaskiya wannan Yola'n akwai shi da nisa". bankai ga idda maganar zucin da nake ba najiyo maganar direba yana faɗin "To nifa iyaka na nan garin bazan karasa can Yola ba waɗan da zasu wuce zasu yi gaba sai su sauka su tari wata motar anan". Ido na waro da mamaki nace "Au bamu iso Yola'n bane?". wata matar da ke gefe na tace "Eh ai bamu iso Yola ba tukun me mukayi ai da sauran tafiya". "Ikon Allah". nafaɗa a fili kana na buɗe marfin motar na fito, direban ya sauke mana kayan mu, a hankali na koma gefen titi kan wani itace na zauna ina rungume da Naseem daya farka yana shirin yin kuka, gyara zama ta nayi da kyau nabuɗe jakata na ciro gorar kunu da na ɗura musu, nabashi yasha kana na kunce Nasmah da naji ita ma tana motsi na bata itama tasha,kana na kara musu da nono, sai da na tabbatar sun koshi sannan na mike na mai da Nasmah na goya ta na ɗauki Naseem... wata mota ce tasharo kwana daga can dagodu sosai sai kuma ta rage gudun dai-dai san da tazo daf da Ni taɗan gotani kaɗan sai ta tsaya. Direban dake tuka motar yazoge glass ɗin motar yaleko ni kana yace "Tafiya ne?". Kai na gyaɗa masa kana nace "Eh". yace "Wani gari". nace "Yola". "Ok shigo ai wannan motar Yola can na nufa yanzu". da sauri na gyara rikon Naseem nasun kuya na janyo akwati na, da saurin sa yafito daga cikin motar ya karɓi akwatin yabuɗe but yasaka kana yabuɗe min gidan baya nashiga kana ya mai da murfin yarufe yakoma mazaunin sa kana yaja motar muka soma tafiya. mamaki ne yakama Ni lokacin da naga Ni ɗaya ce cikin motar babu kowa babu ko fasinja acikin motar. abun da tadaɗa bani mamaki ma shine motar batayi kama da na fasinja ba,ban kuma lura da hakan ba sai da nashiga motar. lafiyayyiyar mota ce irin na shiga kawai. shiru nayi ina bin motar da kallo motace mai kyau tabbas batayi kama da motar ɗiban fasinja ba. wani irin tsalle zuciya ta tayi dai-dai lokacin Naseem da Nasmah suka zabura lokaci guda suka kankame ni Naseem dake rike a hannuna yajuya kansa tare da kife fuskar sa a kirjina sai ya shiga sauke numfashi, leka fuskar sa nayi sai naga yana bacci, Saukar numfashin Nasmah nakeji a bayana itama a hankali. Idanuna na lumshe tare da kuma buɗe su, "Innalillahiwa'inna'ilaihirraji'un" nafurta kan laɓɓana batare da nasan da fitowar sa ba. yayin da yanayin da nake jinsa a tun motar farko da na rika ji ya karu matuka, sai dai har lokacin nakasa gane kalar yanayin. haka mukayi ta tafiya yayin da tsalle da bugawar da zuciya ta take ke karuwa a kowani dakika,jin zuciyata nacigaba da azalzala ta sai nashiga nanata kalmar Innalillahiwa'inna'ilaihirraji'un. tafiya muke tafiya mai nisar gaske nayi mamakin ganin garin Yola da irin wannan nisar wajen karfe 6 muna kan hanya can muka iso wata kungurmin daji danake hangosa daga nan kan hanya. a sannu direban yaɗan sakai ta godun da yake yafaka motar a gefen titi sakamakon kiran da ya shigo wayar sa, yajuyo ya kalleni yace "Bari na amsa waya ina zuwa". jiki a sanyaye nace masa "To". ya sauka da sauri ya mai da murfin ya rufe, yaɗa masa can gefe yana wayar, gabaki ɗaya hankali yakuma mummunar tashi tsoro mai firgitarwa ya lulluɓe ni, bugu da kari ganin yanayin da Naseem da Nasmah suke ciki duk da bacci suke amma sai zabura suke suna kankame ni. daɗa kankame ƴaƴana nayi ina ambaton sunan Allah, magana yake yana kallon motar a hankali nakai hannuna nayi kasa da glass ɗin gefen da nake a hankali batare da na saukar dashi duba. naɗan maso jikin kofar na kasa kunnena.. A hankali nake jiyo sautin maganar sa duk da bana fahimtar abun da yake faɗa sai dai yanayin iska dake kaɗa wa yana ɗan ɗibo maganar zuwa inda nake. "Yes oga yaukam nayi babban kamu wata yarin yace da ƴaƴa biyu a ajiye min kuɗi na ayi musu kyakkyawar ajjiya ina zuwa a damka min su, ina faɗa maka rai uku da babba da yara kananu guda ku a dana min kuɗi na kawai munkusa isowa,ina faɗa maka yarin ya ce gatanan inaga budurwa ce da yara guda biyu ai yau kam fitar sa'a nayi, haba oga ai kai ma kuɗin da zaka karɓa akan su bana wasa bane jinin su ma kaɗai makudan kuɗi ne bare sauran sassan jiki". wani irin masifaffen tsalle zuciyata tayi tamkar zata faso kirji na ta fito, da karfi na dafe kirji na yayin da kai na yayi wani irin mummunar sarawa, jikina yaɗauki ɓari kamar mazari kallon mutumin nake cikin matukar firgita da masifaffen tsoro. Naseem na kuma rungume wa da karfi a kirjina, cikin matsanancin tsoro hawaye yafara sauka a idona, a hankali na masa ɗaya ɓarin hannun na rawa naɗaura jikin murfin motar na buɗe a hankali, nazuro kafafuna waje namike, na mai da marfin a hankali har lokacin yana tsaye yabaiwa motar baya yana ta kan wayar, cikin sanɗa narika tafiya ahankali-ahankali narika tafiya na gangara gefen titi nashiga cikin dajin dake gefen titin a hankali cikin sanɗar narika shiga cikin dajin. ina shiga cikin dajin narika gudu ina kankame da Naseem gudu nake babu ko kakkautawa da iya kafina ban kuma sanin inda nake jifa kafata cikin tsananin tashin hankali mara misaltuwa, gudun nake da iya karfina na sai da na isa gindin wata ƙatuwar bishiya kafin natsaya a gun na rakuɓe jikin bishiyar, ina mai da numfashi, muryar mutumin najiyo daga can yana faɗin "Ke ina kike ina kika shiga?". cikin wani irin kaɗuwa da firgici nadaɗa rungume Naseem na rakuɓe sosai ajikin bishiyar, jikina na cirawa... Ina jin Muryar sa yana ta matsowa in da nake daga in da nake ɓoye ina kallonsa ya gangaro har yazo kusa da ni yana ta waige-waige yana cigaba da faɗin, ke Ina kike. numfashi nane yasoma yin sama-sama tamkar zai fice a jiki, ganin sa daf da Ni. dubana nakai kan Naseem da ya buɗe ido yana kokarin yin kuka kai nashiga girgiza masa tare da ɗaura hannuna kan bakin sa narufe da karfi. mutumin ya ɗau lokaci agun yana dube-dube kana yayi tsaki tare da faɗin "Kash ga samu ga rashi taya ma akayi har tafita ban ganta ba". yakuma jan dogon tsaki yajuya yakoma gon motar sa. ina ganin haka nakuma sa gudu narika kusawa cikin dajin, gudu ne irin na ceton rai ko ina ce rayuka, bana ko ganin gabana. ga lokacin tuni guri yasoma yin duhu sai dai hasken farin wata daya haske ko ina... Tuntuɓe nayi da wata katuwar kututture da bansan tana gaba na ba,nayi luuu zan faɗi sai nayi baya tangal-tangal kaɗan yarage na faɗi da baya, Naseem ya suɓuce a hannuna yafaɗi kasa timm,bayan da nayi kuwa hakan yayi sana diyyar kan Nasmah ya garu da jikin wata bishiyar dake baya na, a tare suka saki kuka Naseem kam tun da yasaki wani irin kara mai karfi tun da yasaki karan nan bai kuma yin motsi ba. cikin tsananin firgici da tashin hankali nayi kasa naɗa go Naseem da ko matsi bayayi na rungume shi a jikina da karfi nashiga girgiza shi da kiran sunan sa, "Naseem Naseem Naseem katashi dan Allah katashi katashi Naseem". narika faɗa ina girgiza shi da kiran sunan shi amma ko motsi baiyi ba, cikin rasa abin yi na zube kasa ina cigaba da girgiza shi, babu ko alamar nunfashi tare da shi, hankali na yakuma mummunar tashi ga Nasmah sai zandara ihu take. wani kuka nasake da karfi ina girgiza shi da karfi, ɗankwalin kai na na ciro nashiga fifita shi ina kiran sunan shi, nan ma shiru rungume sa nayi da karfi ina faɗin "Naseem ka tashi dan Allah kada ka mutu, ka kabuɗe idon ka dan Allah Naseem kada ka mutu Naseem Naseemmmmmmm". Nafaɗa da karfi cikin muryar kuka... Duk yan da nayi ta jijjiga shi da kiran sunan sa da kuma yi masa fifita yana nan a inda yake babu numfashi a jikin sa,nayi ta kuka kamar raina zai fita ina kankame dashi,kamar an zabure Ni na ɗagosa da sauri na shin fiɗa shi a kasa na mike da sauri nashiga duba gefe da gefe na ko zan ga ruwa na yayya fa masa ko Allah zai sa ya tashi, bazan mance ba ɗan goggo Hauwa yataɓa yin irin yan da Naseem yayi sai dai shi ba faɗuwa yayi ba rashin lafiya yake sai numfashin sa yaɗauke lokacin sun zo gidan Inna sai naga Inna ta ɗibo ruwa tayi ta yayyafa masa sai ya farfaɗo numfashin sa ya dawo. da gudu nayi gaba narika ɗan zaga gurin babu alamar ruwa agurin, da gudu na dawo in da yake na ɗago shi nashiga hura masa iskar bakina a fuskar sa, narika hurawa ina kiran sunan shi. mun kai minti 30 agurin ina abu ɗaya babu kuma sauyi, da sauri nasaka bakina kan bakin sa narika hura masa iska da karfi, wani nannauyar numfashi ya sauke tare da sakin kuka mai karfi ya kankame Ni, nima kukan na kuma fashewa da shi na rungume shi ina faɗin "Alhamdulillh Allah na gode maka". da sauri na kunce Nasmah da take ta kuka tun ɗazu na haɗe su duk na rungume. nayita rarrashin su sai da naga sun yi shiru, nakuma basu abincin su nan ma sai da naga sun koshi, kana na ɗago Naseem wannan karo shi na goya shi narike Nasmah a hannu. A sannu narika waige-waigen gefe na nashiga kallon kungurmin dajin da muke ciki ciki kaɗuwa da tsoron ganin guri yagama rufe wa yayi duhu ga daji bakajin motsin komai sai na tsuntsaye da wani irin muryoyi da numfarfashin abubuwan da ban taɓa jin irin suba, da sauri na juya hanyar da nafi tunanin tanan nabiyo nashigo cikin dajin nabi da sauri narika tafiya sai dai abun mamaki nayi tafiya mai tswon gaske ban ga alamar titi ba, firgici da tashin hankali yaku baibaye ni ganin kamar daɗa kusuwa cikin dajin nake ga wasu abubuwa masu firgitarwa da razanar wa da nake ta gamuwa da su a hanya. da sauri na ja na tsaya ganin wani abu saman sa haske kasan sa duhu mai tsoratar wa, cikin firgici da kiɗi ma najuya da sauri mai haɗe da gudu na koma da baya jikina na cirawa, sai da natafi da nisa sannan na tsaya, gefe da gefe na na kalla ina tunanin ta wace hanya ce nabiyo nashigo cikin nan, a kiɗime na kama wata hanyar ta daban wan da nake ganin ko ita zata fidda ni bakin titi, nayita tafiya har na godewa Allah amma ita ma babu alamar titi a gaban ta. nakuma canza wata hanyar haka nayi yawo har guri yagama rufawa gaba ɗaya.. Zuwa yanzu kam kuka na fashe da shi ina ambaton sunan Allah duk inda na juya gabar da yamma kudu da arewa daji ne. Wani kututture da ke gefe da in da nake tsaye ina iya hango shi sabo da hasken farin wata na isa na zauna a kai tare da kuma sakin kuka cikin muryar kuka mai haɗe da tsantsar tashin hankali da kaɗuwa nake faɗin "Ya Allah kakashe ni na huta Allah ka tsiratar da waɗan nan yaran Allah ka gani basu ai kata laifin komai ba, ya ALLAH ni ka ɗauki raina su ka tsiratar da su kasan basu ai kata komai ba". kukana ne ya tsananta lokacin da na ɗaga kai nakuma bin dajin da kallo, najima sosai a zaune naci kuka har na godewa Allah...........!★ Mommyn Twins ce Ina zaune a kan icen shiru ina ta girgiza su Nasmah dan bana so su rika kuka dan idan suna yi sai na rika jin motsin abu kamar yana tahowa in da muke, ina nan zaune babu alamun bacci ko gyangyaɗi a idona sai tarin ɗinbin tsoro da tashin hankali....... ganin guri ya ɗan yi haske ba kuma hasken farin wata ba, hakan ya tabbatar min da gari ne ya waye wato dai mun kwana a zaune kenan. a hankali na mike tsaye ina bin kungurmin dajin da kallo, duba na nakai karkashin kututturen da muka kwana a kai jin motsi da huci, a kiɗime cikin kaɗuwa nayi baya da sauri yayin da hantar ciki na yayi wani irin kaɗawa ganin ƙatuwar maciji tana fitowa daga karkashin iccen, juyawa nayi da gudu narika gudu cikin matsanancin tashin hankali sai da nayi gudu mai nisan gaske kana na tsaya, ina maida numfashi da gyara rukon Nasmah da tuni suka saki kuka dukan su, najuya ina wai gen baya na. kukan nima na sake nakasa rarrashin su sai kukan dukan mu muke. a galabaice na zube kasa na zaunar da Nasmah a kasa kana na kunce Naseem shima na ajiye shi gefe har lokacin duk kanin mu kuka muke ina binsu da kallon tausayawa, sai na rungume su duka nakuma fashewa da kuka. sai da nayi kuka mai isata kana na ɗago su na basu abincin su, sai dai na san basu koshi ba dan har lokacin basu dai na kananun koke-koke ba tabbbas dole bazasu koshi ba banciba bare su su samu abinci a jikina, ni kai na yunwar nake ji mara misaltuwa. wasu zafafan hawaye na share kana na mike tsaye, ina ɗan kalle-kallen in da muke zaune, gindin bishiyar mangoro ne ga mangorori sunata rito kasa-kasa, na ɗau wani kara da ke gefe na a kasa na mika hannu nayi tsalle na buga mangorori guda uku suka zubo kasa, ɗaya ja biyun kuma duk basu yi ba haka na ɗauka nayi ta shan su kaf sai da na shanye su. kana nayi taimama, waige-waige nashiga yi dan bansan inane gabar ba,ina zan fuskanta nagabatar da sallar ba, sai kawai na nafiskanci gabana na gabatar da sallar asuba. ina idarwa na kuma goya Naseem da tun jiya da ya faɗi jikin sa yayi zafi rau har kuma yanzu jikin nasa da zafi sosai, sannan na ɗauki Nasmah muka cigaba da tafiya... Munyi tafiya mai nisa jin na gaji nakuma tsayuwa na huta, kana na kuma ci gaba da tafiyar, wunin ranar haka na wuni ina tafiya idan nagaji da tafiyar duk inda na samu sai na zauna sai dai ban kuma yar da na zauna kan itace ko sunkuru sosai ba guri mai ɗan fili nake samu sai na zauna, a duk inda nayada zango na kwatanta lokaci kawai nake sai na gabatar da sallah. ko yanzu ma a wani guri mai ɗan fili na zauna bayan na idar da sallar isha ganin guri yayi duhu sosai sai hasken farin wata, ina rungume da Naseem da Nasmah, cikin tsananin tsoro da kaɗuwa na daɗa rungume su jin matsi da kukan wasu abubuwa cikin wasu irin muryoyi daban-daban. idanuna na rumtse ina ambaton sunan Allah, zuwa can da daɗewa sai na rage jin sautin muryoyin, a haka dai har gyangyaɗi yarika ɗan fizgata nayi ta ɗan gyangyaɗin har gari yawaye... Washegari ma haka na tashi nayita tafiya in na gaji na huta, yunwa kishin ruwa zafin rana, zuwa yanzu kam jan kafata kawai nake Nasmah da Naseem sai kuka suke nakuma san suma yunwar ce ke ɗawai niya da su. yunwa da ta addabe ni tafiyar ma da kyar nake iya yin ta zuwa yanzu kam duk wani bishiyar da na haɗu dashi idan naga yayi min kama da na ci sai na sinka naci. nayi tafiya har na gaji kafata duk sunyi bororo kaya sun kwakkwar janeni bani kaɗai ba hatta su Naseem da kwarjanin kaya a jikin su dan idan muna tafiyar naga wani abun tsoro zan sa gudu ta sana niyyar hakan zasu faɗi ko kuma mu faɗi tare haka zan tashi naɗa ga su na rarrashe su sai in sunyi shiru muka cigaba da tafiyar... Tafiyar da bansan ina muka dosa ba tafiyar da har yanzu bata ɓulle dani titi da nake sammanin tana gabana ba, tafiyar kunci da wahala.. Yau kwanan mu biyar a cikin dajin nan, nagama galabai ta na susucewa nafita hayyaci na, yunwa kishin ruwa zafin rana, baci ba sha ba wanka haka mukayi ta rayuwa acikin dajin nan har na kimanin kwanaki biyar. a hankali nake jan kafata da ta kumbura ganin dare yayi ina ta ɗan sauri dan mufita a cikin sun kurun da muke mu isa ɗan sararin da nake hangowa a can a gabana, da kyar na karaso gun na sauke su Nasmah muka yada zangon mu agun, rukon su na kyara kan kafata cikin sansanin tausayin su, na zuba musu ido, sun rame sun dishe sun dawo abun tausayi. ina nan zaune yunwa ya hanani sakat, suma sai kananun kuka suke wan da nasan kuma na yunwa ce, daƙyar na rarrashe su sukayi bacci, niko kasa yin ɗan gyangyaɗin da nake yi ɗin ma nayi saboda tsabar yunwa, haka na raba dare ina zaune.. koda gari ya waye kuwa nacigaba da aiki na wato tafiya.... Nayi taganin abubuwa masu razanar wa da firgitarwa idan naga wani abun ma kasa ihu ko niman gudu nake sai dai na rufe idanuna da karfi ina ambaton sunan Allah, nakuma sadakar da cewa rayuwa ta dana ƴaƴana yazo karshe... Allah sarki rayuwa dani da ƴaƴana mun sauya kamanni mun rame mun fita hayyacin mu mun dawo wasu irin abu da kama, mun dawo tamkar mahaukata, Zuwa yanzu karfina yagama kare wa ɗaukan su yana so yafi karfi na, idan na ɗauke su mukaɗan yi tafiya kaɗan sai naji numfashi na nayin sama-sama idan na ɗan tafi kaɗan sai na ajiye su na huta sosai kana mukuma yin gaba. Yau kimanin sati biyu kenan muke rayuwa acikin dajin da nake mana fatan mutuwa dan na tabbata ita zatafi zame mana hutu da wannan rayuwar. cikin jan kafa da ɗan sauri na nufi bishiyar mangoro danake hangosa can sakanin mu daɗan rata dashi, da sauri narika jan kafata dan rabon da na haɗu da bishiyar mangoro ko wani abu mai zaki na kai kwana biyar, sai dai naci ƴaƴan itace mai ɗaci ko tsami ko burti. daƙyar na isa gin din bishiyar ina sauke numfashi da sauri na sauke yaran kasa naɗau san da narika kaɓe mangoron sai da na zubo da su da yawa kana na zauna na tattaro su gaba na,nasunku ya sha ba ko kakkautawa har jikina na ɓari, ina kallon su Naseem suka ɗauka waɗan da ke kusa da su, suna ta gwaguya ban ko hanasu ba dan suma nasan kalar yunwar da nake ji shi suke ji. ina gama sha naji cikina yawani irin murɗa wa na kwanta a kasa, na da fe cikin nayita murkususu har da hawaye. najima zube a kasa ina juyi can naji yaɗan sassauta min na mike na ɗau kesu muka cigaba da tafiya..... Kamar mahaukata duk kayan jikin mu yayi matukar datti bazaka iya shaida wani irin kalar kaya bane a jikin mu,sabo da tsabar datti, nawa kamma duk ya yayyage daga kasa. tun wannan mangoron da muka sha bamu kuma samun wani abun ciba a hanya ba sai da muka kuma tafiyar kwana biyu, daga can da nisa sosai na hangi wani katon dutsai mai girma sosai gefe da dutsai ɗin wasu bishiyoyi ne ajere, daga in da nake tsaye ina jiyo wani irin sauti mai kara da kugi mai karfi sosai duk da kuwa ina juyo sa daga can da nesa, cikin sauri da fatan Allah yasa bishiyar abun cine nakara sauri duk da azaba da zugin da kafafuna keyi, nanufi gurin dutsai da bishiyoyin nan suke. duk da dai zuciya ta ciki da zullumi da tsoron jin ina daɗa matso in da kara da ƙugi wato irin sautin gudun ruwa yake, amma ban fasa nufar in da bishiyoyi da katuwar dutsai ɗin nan suke ba, kuma nan nake jiyo kugi irin kugi mai amon sauti irin na ruwa mai karfi sosai ɗin nan. a sannu narika tafiya ina yi ina huta wa har na iso kusa da dutsai da bishiyoyin nan, wani irin juyawa da tsara wa kaina yayi hango wani katon kogi mai girman gaske, cikin ɗan ɗar-ɗar na karaso jikin dutsai ɗinan wan da can gaban sa kuma katon ruwa ne yana gudu da sautin kugi mai karfin gaske. koton kogi ne mai girman gaske ko karshen gaɓar sa bana gani, ruwane mai girman gaske ko a TV ban taɓa ganin irin wannan ruwa mai girman gaske haka ba. gefe da dutsai ɗin kuwa wasu bishiyoyi ne lif-lif-lif masu kyau sai dai da yawan bishiyoyin ban san ko bishyar menene bane gasunan da tarin ƴaƴa a jikin su wasu jajaye wasu koraye, daga cikin bishiyoyin kuwa akwai na mangoro gwaiba dabino kwara kwakwa da kuma tupa, gasunan kasa-kasa. gindin bishiyoyin kuwa yashine fari soll amalale agurin kamar an share gurin babu ko datti har zuwa bakin gaɓar ruwan. daga gurin bishiyoyin zuwa bakin gaɓar ruwan da ɗan tazara kaɗan, kafin ai nihin babban ruwan akwai wani ruwa a ɗan gaban bishiyoyin sai dai shi ɗan kaɗan ne da alama dai ruwan idan yayi yawa yana haurowa har gurin idan ya koma kuma sai ragowar ya tsaya a ɗan wannan ramin. ruwan fari soll kamar babban ruwan kogin nan da yake gudu.... A hankali natako zuwa gun yashin nan wato karkashin bishiyoyin nan, na sauke su Naseem na zaunar da su, da sauri cikin jin matsananciyar kishin ruwa na nufi in da wannan ruwa ɗan kaɗan ɗin yake na sun kuya na saka hannuna narika ɗiba ina sha, sai da nasha na koshi,kana narika ɗibawa da hannuna ina zuwa in da su Nasmah suke na basu suka rika sha, haka narika kai wa da komowa ina ɗiba ruwan a hannuna ina kai musu suna sha, haka narika yi har sai da na tabbatar da sun koshi,kafin na kyale su. na koma gurin ruwan nayi al'wala na dawo in da suke nayi sallar azahar da nake tunani yanzu lokacin sa yayi. ina idarwa na mike lokacin rana yafito sosai na ɗago Naseem na tuɓe masa kayan jikin sa da yayi wani irin datti dattin har ya wuci misali, na ɗauko shi muka taho bakin wannan ruwan da muka sha nakuma yi al'wala da shi, na saka hannu cikin ruwan kasan cewar rana yafito hakan yasa ruwan yaɗan yi ɗumi sai narika ɗiba ina wanke masa jikin sa na wanke shi sosai kana na ɗago shi na goyashi, na ɗauko Nasmah ma itama na tuɓe mata kayan ta itama da yayi matukar datti kamar bana ɗan adam ba, na wanke mata jikin ta sosai kana na rungume ta muka koma gindin bishiyoyin, nan da nan kuwa sukayi bacci ina zaune rungume da su,tabbas datti wani sashi ne mai hana ɗan adam sakewa da jin daɗi ɗan rage musu dattin jikin su nayi sai gashi sunyi bacci cikin kankanin lokaci. ɗankwalin kai na, na cire na shin fiɗa a kasa kana na kwantar da Nasmah dake hannuna, sannan na kunce Naseem na shinfiɗa zanin goyon su na kwantar dashi sannan na ɗago Nasmah a kan ɗankwali na na mai data kan zanin goyon kusa da shi, hijabina na cire na rufe su da shi kana na ɗauki ɗan kwali na na ɗaura. gurin ruwan na koma na wanke musu kayan da na tuɓe musu na shanya kan yashin gurin, kana na tuɓe kaya na na wanke jikina duk da ba soso ba sabulu amma naji da ɗin saka ruwan a jikina. na wanke kayan su da na tuɓe musu na shan ya kan yashi. sannan na dawo in da suke na kwanta a gefen su wani nannauyar bacci yaɗau keni. bacci ne mai nauyin gaske yaɗauke mu dukan mu ban farka ba sai can dadaɗe wa koda na tashi na fahimci cewa yamma tayi sosai dan guri yayi duhu, al'wala nayi nazo na gabatar da sallar la'asar, ko da na idar tagumi nayi a gaban su na zuba musu ido, sun rame sun dishe wagasu kananun kuraje da suka fito musu duk jiki, ido na rumtse yayin da tausayin su ke daɗa rasa ni har sai da wasu zafafan ƙwalla suka zubo min batare da nasan da fitar suba. nakai hannu nashare ina cigaba da kallon su a raina nake faɗin "Ya Allah ka tseratar da su ka fidda su a cikin wannan kungurmin daji"... A hankali na mike tsaye jin cikina na murɗan yunwa na sinko ƴaƴan itatuwa da yawa wanda na sani har da wan da bansan su ba duk wan da na sinko na gusura najisa da zaki sai na kama ci, nan su Nasmah suka farka da kuka na ɗago su na basu abincin su suka sha wanda sai dai susha ne kawai bawai kodun ya koshar da su ba. suna rungume a jikina a haka guri yarufa sosai lokacin tuni sun koma bacci sai nayi musu addu'a na kwantar da su naje nayi al'wala bayan na idar da sallar magriba da isha sai na kwanta gefen su. Washegari naji daɗin bacci a gurin sosai bakamar na sauran kwanakin da mukayi a cikin dajin ba,tabbas nan gurin da muke zaune wata rahama ce dan kuwa anan muna samun ruwan sha da ƴaƴan itatuwan da zance,da ruwan da zanyiwa ƴaƴana wanka da kuma ni kaina duk da bada soso da sabulu muke yin wankan ba. da waɗan nan abubuwan mukayi ta rayuwa a gefen ruwa har na tsawon wata guda. gurin ya zame mana tamkar gida kuma ɗaki, a gurin na kan iya ajiye su na ɗan zaga ta bayan bishiyoyin nan na sinko mana wasu kalar kayan itatuwan nakawo mana dan yanzu har su Naseem ma ci suke mu samman abu mai ɗan laushi....★ Zaune muke bayan na musu wanka suna kan kafata ina ta yi musu wasa sai ɓarkewa da dariya suke, cikin dabara na sauke su namike naje nayi wanka kayan su dana wanke musu ɗazu da nayi musu wanka nashan ya kan yashi yabushe na ɗauko nazo na sa musu. ina zaune a gefen su Naseem ya lankwasa kafar sa ya rarrafo yazo in da nake, cikin tsananin farin cikin ganin yau yaron ya fara rarrafe nashafa kansa ina dariya da faɗin "Iye lallai Naseem wato kayi wa Nasmah wayo ko kai ka fara iya zama shine kuma zaka riga ta iya rarrafe ko, amma dai zaka barta ta iya da wuri itama ko?". baki yawashe kamar yasan abun da nake faɗa, na kama kuma tun Nasmah ina faɗin "Kema ki dake kinji kada yarika yi miki wayo da yawa". nayi maganar cikin shauki, itama dariya ta saka min duk na rungume su ina dariya, a take kuma naji wani kuka yazo min sai kuma na fashe da kukan..... cikin ƴar dar Allah bayan sati ɗaya kuwa Nasmah itama ta fara rarrafe. tun da naga rarrafen su yafara yin kwari, sai bana yin nesa da su dan gudun kada su rarrafa suje su shiga cikin ruwan nan idan zan je tsinko mana abun da zamuci sai na ɗauke su mu tafi tare, ko bacci nake ji har idan idon su biyu bana yar da natafi na barsu su idan su biyu, dan duk lokacin da naje na musu wanka Naseem yarika zillewa yana son shiga ruwan yarika bori da shure kafafu wai sai dai na barshi yashiga ruwan, shi yasa nake jin tsoro kada wata rana nayi bacci yace zai je yashiga ruwan bugu da kari ma zai iya tunkarar babban kogin nan, to haka zan yi ta zaman gadin su har sai sunyi bacci kafin nima nayi..... Zaune nake na buga uban tagumi nayi shiru ina lissafa kwanakin da mukayi a cikin daji tabbas yau idan ban mance ba kimanin watan mu biyu kenan acikin dajin, wasu hawaye ne suka zubo min na share su. Ikon Allah haka zamuyi ta rayuwa a cikin daji har mu mutu karshe namun daji sucinye mu, tausayin kaina da na ƴaƴana ya kamani sai na rungume su na fashe da kuka. ganin sunyi bacci na shin fiɗa musu abun kwanciyar su wato zanin goyon su, na janyo hijabina na lulluɓe su, na mike na soma tafiya.. kallon sama nayi hadari ya haɗu bakikkirin daga can kasa sai walkiya ake da rugugin tsawa da alama dai anata zabga ruwa daga can da nisa, ina tsaye ina tsinko abun da zan ci daga can nesa narika jin kugin ruwan nan yana karuwa sosai ba kamar nasauran kwanaki ba ƙugi ne sosai mai matukar amon sauti sosai. da sauri na juya na fito daga cikin bishiyoyin na nufi in da su Naseem suke kwance cikin hanzari. Daga can na hango ruwan yana wani irin gudu da kugi daga can da nisa yana wani sama da kasa. Huff na ɗaga Nasmah na goya ta kana ɗauki Naseem da gudu na juya ganin ruwan yana haurowa a hankali inda muke yanata taruwa a hankali har ya wuce idon sawu na, daga can cikin kogin kuma yana wani irin gudu yana yin sama da kasa sai ruwan ya haɗu da junan sa ya fansalu sai yayi sama sannan ya koma kasa. gudu nake da iya karfi na nayi bayan dutsai cikin sansanin tashin hankali galin ruwan ya iso inda muke zama ya mamaye gurin wan da yake gudu daga can kuma sauran kiris yakaraso, bayan dutsai da na ɓoyen ma tuni ruwan ya iso har gurin, cikin kaɗuwa da tashin hankali nasoma hawa kan dutsan da ko a mafarki ban taɓa tunanin zan iya hawan sa ba sai gashi na haura kan sa da goyo da kuma wani ɗan a hannuna can kuma saman sa sosai. kan kace me ruwan yataho da wannan kugi da ambaliyar da yake, gurin da muke zama yadawo tamkar cikin ainihin kogin hatta bishiyoyin nan sai da ruwa yahaye kansu, duk da girma da tsawon da dutsai ɗin nan yake dashi sai da ya kusa haurowa sama in da nake tsaye jikina na cirawa, rumtse idanuna nayi nakuma buɗewa cikin ruwan da yake wani irin gudu da kugi, ina ambaton sunan Allah, yau kam nasan mutuwa ce yazo mana babu makawa ruwa ce zata zamo ajalin mu,zata tafi da mu mu kuma mutu a cikin ta. kankame ƴaƴana na kuma yi nagama sadakarwa na mika wuya ga mutuwa gaba ɗaya. wasu irin halittun ruwa narika gani daban-daban wani abun ma idan nagani rufe idanuna nake da karfi har sai ya wuce kafin na buɗe,haka sukayi ta wucewa a kan ruwan, wani abun da yadaɗa firgita ni da bani tsoro daga can najiyo guɗa mai karfi a can tsakiyar ruwan guɗa mai tsawon gaske babu jan numfashi ko sauke wa, ido na zuba sosai daga can in da guɗar ke tashi sai dai banga komai ba sabo da sakanin mu da nisa kuma da alama daga can kasa abun ke wuce wa. sai narika jin kamar iska tana jana kuma karfin iskar tacikin ruwan ne,kuka na fashe dashi na durkushe kan dutsai ɗin na kankame jikina,ina ambaton sunan Allah. har lokacin ban fasa jin iska na kokarin jana ba, a hankali guɗan da ake yarika raguwa alamun yana yin nesa da ni, iskar da ke jana kamar zai faɗar dani cikin ruwan sai yarika sassauta, lokacin da na dai na jin sautin guɗar nan gaba ɗaya iskar ta tsaya. abun tun sassafe sai yamma can kafin ruwan yafara sassauta gudun da yake, yana sassauta yana yin kasa-kasa, a hankali yarika yin kasa yana wuce wa har ya dawo in da yake, Numfashi mai cike da zallar tsoro na sauke a sannu narika bin gurin da kallo har zuwa gurin da muke zama, yashin ya daɗa wankuwa yayi fari soll sai dai har lokacin da jikan ruwa sosai a hankali nafara kiciniyar sauka daga kan dutsan nayi matukar mamakin yadda akayi na iya hawa saman dutsan, daƙyar na iya sauka kasa. a hankali narika takawa in da kafata har yana lumewa cikin saka sabo da har lokacin da dam shin ruwa, a hankali na matsa can gefe in da shima akwai damshin sai dai ba kamar in da muke zama ba. ranar a nan muka kwana cikin ciyawa, sai dai ban yar da na rumtsa ba dan gani nake kamar ruwan zai dawo.... Washegari da safe gurin ya daɗa sha ya tsantsame sai dai har lokacin da ɗan damshin sai dai ba kamar na jiya ba, sai da rana yafito sosai kana a hankali na ɗauko su Nasmah muka dawo gurin zaman mu, ido na kurawa kogin nan ganin yadawo yan da yake da, kamar bashi bane jiya yayi ta hauka Allah mai iko. ɗan kwalin kai na na kunce na shin fiɗa a kasa kana na zaunar da Naseem a kai ina faɗin "Zauna kada ka sauka kasa kaji gurin da sanyi". da sauri na kunco Nasmah da take ta musu-musu tana kuka a abaya, na zauna na basu abincin su, sai dai har lokacin bata fasa kananan kuka ba, jijjiga ta nashiga yi ina faɗin "Yi hakuri Nasmah nasan wan ka kike so kuma nasan ruwan nan akwai sanyi kibari rana yadaɗa yin zafi idan ruwan yayi ɗumi sai na muku". nayita jijjiga ta. zuwa can an jima jin rana yadaɗan yi zafi sosai sai na tuɓe su na dubi Naseem da ke zaune yana ta wasa da yashin gurin nace "Zauna na fara yi mata wanka sai na ma ka ko". na mike da ita a jikina na isa gurin ruwan da muke wanka, ruwan yada ɗa yin fari soll, kasan cewar rana ya taso ruwan har yana kashe ido sabo da tsabar hasken da ya kara, a hankali na fara yi mata wankan ina yi ina kawar da kai na daga kallon ruwan saboda kashe min ido da yake, tamkar hasken ranar a cikin ruwan yake. koda na gama yi musu wankan. babu jimawa sukayi bacci, mikewa nayi na koma gurin ruwan domin yin al'wala, na sun kuya ina ta kare fuska ta da hasken rana ke haska cikin ruwan yana kashe min ido, na saka hannu cikin ruwan a hankali na ɗibo na fara yin al'walar, na kuma mai da hannuna a karo na biyu, da sauri na ciro hannun jin na taɓa wani abu, sai kuma na mai da hannun a hankali jin kamar dutsai ne na taɓan, a raina nake ai yana cewa ai dutsan yashi ne, na cusa hannuna nakuma ɗibo ruwan sai na haɗo da yashi da wani farin dutsai, ina ɗago hannuna hasken rana ya haska dutsan tamkar wutan lantar ki mai hasken gaske. da sauri na rumtsa idanuna jin hasken har cikin jijiyoyin idanuna, cikin hanzari na watsar da yashin gefe ina mammatse idanuna, nayi al'walan da sauri na bar gurin... koda yamma tayi da nazo yin al'walan la'asar lokacin rana tayi sanyi hasken ruwan yaɗan ragu, ina saka hannuna cikin ruwan nakuma ɗauko dutsai ɗin, A hankali na ɗago shi narika juyashi a hannunna dutsan fari soll mai kyau da shi sai kyalkyali yake duk da kuwa babu hasken rana, narika kallonsa gwanin ban sha'awa. A hankali na mika hannu na ɗauko ɗayan da ɗazu nayi wurgi da shi na haɗa su ina ta juya su cikin sha awa, nakuma saka hannuna cikin ruwan nayi ta laluɓo duwasun ina ciro su sai da naciro guda takwas na haɗa da biyun hannuna suka zamo guda goma, bayan na gama al'walar na koma gun su Nasmah a kan abun goyon su na zuba duwasun, ina zubawa kuwa da sauri har suna rige-rigen ɗauka sukayi ta wasa da shi, nima ina idar da sallar na zauna nayi ta tayasu wasan da duwasun gwanin ban sha'awa da kyau da ɗaukar ido. dariya nayi ganin yanda suke wasa da duwasun su ɗauki wannan su wurga sai subi sukuma ɗauko wa, nace "Kuma yayi muku kyau ko ai dutsan mai kyau ne nima wlh yayi min kyau kuyi wasan ku da shi". nafaɗa da murmushi ina daɗa tura musu duwatsun gaban su... Washegari ko da rana yafito dukan su na kwasa naje musu wanka Nasmah na goye sai na fara yi wa Naseem ko da na gama mishi, sai na saka hannuna nayita laluma cikin ruwan can na ciro dutsai ɗin guda ɗaya na dunkule shi cikin hannuna na cusa masa cikin hannunsa ina faɗin "Gashi na karo muku abun wasa dun kule shi a hannunka kar ya kashe mana ido". na kunce Nasmah na goya shi itama nayi mata wanka kana na laluɓo mata guda ɗaya na saka mata cikin hannun ta nace "Kema ga naki".....★ Zaune muke muna cin kayan itatuwan dana sinko mana shiru nayi tare da kasa kunne daga can da nisa nake jiyo muryar kukan shanu, da sauri na mike tsaye ina cigaba da baza kunnena ina son gane in da kukan shanun yake fitowa, duk da daga ji yana da nisa da mu sosai, wani irin farin ciki ne da murna ya lulluɓe ni, dan na tabbata shanu bazai zauna shi kaɗai cikin daji ba sai da mutum. cikin tsananin farin ciki da murna na sunkuya da sauri naɗau ki Nasmah ina faɗin "Kuzo muje naji kukan shanu a tacan wata kila mu sami ɗan uwan mu bil adam a gurin". ina ɗago zanin goyon su duwasun da suke wasa da shi suka zubo kasa, banko bi ta kan su ba na goya Nasmah da sauri na ɗau Naseem da sauri nasoma tafiya. har nakusa fita daga cikin bishiyoyin sai na juyo ina juyowa kuwa, na hango duwasun suna wani irin walkiya kasan cewar lokacin rana yafara tasowa, Naseem dake hannuna kuwa tsalle yarika yi yana nuna duwasun da hannu yanata kokarin zame wa a hannuna, murmushi nayi nace "Oh Naseem dutsunan wasan ku ko bari naje na ɗebo muku". na juya da sauri na ko ma gurin ɗankwalin kaina na ciro naɗibi duwasun duka na zuba cikin ɗan kwalin na ɗaure na rike a ɗayan hannuna, na mike da sauri muka kama tafiya. ta in da nafi zato da tunanin tanan kukan shanun ke fita na ɗau hanyar da sauri. sai dai munyi tafiya mai nisan gaske amma ban ga wani alamun shanukai ba hasali ma kukan su da nake ɗan ji yanzu na dai na, har na fara tunanin wata kila ma kunnena ne yajiye min ba dai-dai ba. a gajiye na ja na tsaya tare da waigawa baya a raina nake faɗin "Zan koma kawai gara rayuwar can ya fiye min na ko ina acikin dajin nan". ga mamakina sai naga nayi nisa sosai dan ko katon dutsai ɗin nan bana hangowa na juya da zummar komawa bakin kogin sai kuma na hakura ganin nayi nisa sosai. gashi kuma yamma ta fara yi sai na zauna kawai a gurin a nan gurin muka kwana washegari da safe ina zaune ina ɗan gyangyaɗi dan jiya ban samu nayi bacci ba dan acikin sun kuru muka kwana, kukan shanun nan irin na jiya shi ya farkar da ni firgigit na nimike da sauri.........!★ *Na jiya da gobe na baku*👌🏻😆 Mommyn Twins ce Zunbur na mike tsaye jin da gaske ba wai ko kunne na bane ke yi min karya kamar yan da jiya nayi tunani, da sauri na ɗauki Nasmah na goya ta, sannan na ɗauki Naseem na rike shi, na ɗauki ɗan kwali na da na ɗaura musu duwatsun wasan su na rike a ɗaya hannuna. cikin sauri mai haɗe da gudu narika bin hanyar da nafi sammani da tunanin tanan ne kukan shanun ke fi. nayi ta tafiya idan naji shanun sun dai na kuka sai na tsaya na huta idan duka cigaba sai na mike da sauri nacigaba da tafiya, haka nayi ta tafiya ina yi ina hutawa duk san da shanun sukayi shiru idan suka cigaba da kukan sai nima nacigaba da tafiya ta in da nake jiyo kukan su daga can nesa sosai. nayi tafiya har na godewa Allah. ina zaune a gindin wata bishi ina hutawa gaba ki ɗaya jikina yayi sanyi dan tun ɗazu da shanu sukayi kuka basu kuma ba, har nafara cire rai da sake yin kukan nasu zunbur na muke jiyo sautin su daga can kasa kuma yanzu nafi jin murtar nasu yafi kusa dani akan na ɗazu. da sauri na mike na soma tafi ɗan tafiya kaɗan nayi da sauri naja burki ganin rami a gabana, in da nake tsaye kuma tudune mai tsawon gaske, dan saura kiris na zurma kafata kasa. daga can kasan shima duk daji ne da bishiyoyi, daga kan tudun in da nake tsaye ina hango shanukai ɗin can da nisa suna ta kiwo kasan cewar a kan tudu nake. kallon kasa nayi mai uban nisa da tsawo "Taya zan iya sauka a nan gurin". nafaɗa ina daɗa kallon kasan. a hankali nafara bin gefe tacan ɗaya ɓarin gefen dama na, ganin tacan ɗin bai kai in da nake tsawo sosai ba, a hankali nafara sauka ina takawa a hankali,sam naki yar da na kalli kasa sai naga ya daɗa yi min nisa kaina kuma sai yarika juyawa sabo da nisan sa, nayi rabin saka daga saunin sai kawai kafata ta sule na zame muka rika gungurawa kasa tuni su Naseem suka saki kara mai karfi, kan kace me Naseem ya suɓuce a hannuna ya ganaga can yafaɗi kasa, Nasmah da ke baya na kuwa mukarika gungurawa da ita, cak numfashi na ya tsaya dan ganin ina kokarin isan kasa da baya kamar an juyani sai kawai na faɗi da gefe a kan hannuna. kara dukan mu muka sake da karfi cikin azabar jin yadda na faɗi kan hannuna tamkar hannun zai ɓalle yabar jikina. nayi-nayi na tashi na gagara tashi nafi minti goma kwance ko kyakkyawar motsi na kasa, ina kallon Naseem yashe a can gefe yana ta zandara ihu, Nasmah ma sai ihu take tana goye a bayana har lokacin... Nayi ta yunkurin tashi na kasa da kyar na kai ɗaya hannuna na kunce zanin goyon ta kwanta gefe tana cigaba da tsala ihu duk jikin ta ya kwakkwar jane, hannuna da na faɗi a kansa na ɗagosa da kyar kana da kyar na iya mike wa zaune. yayin da hannun da na faɗi a kansan ke min wani irin zugi da raɗaɗi, da kyar na yunkura na mike ina ɗingishi nazo gun da Naseem yake kife a kasa yana ihu, na zauna na ɗago shi da ɗaya hannuna mai lafiyar, nashiga kakkaɓe masa jikin sa ina jijji gashi, shima duk ya kukkuje a. Nasmah ta rarrafo tana kuka ta zo in da muke na janyo ta na cigaba da rarrashin su, duk abun da nake cikin dauriya kawai nake dan nima duk jikina a kukkuje yake,zafin raunukan jikina bai kai na hannun da na faɗi a kan sa ba. duk raunukan jikin yaran sai jini yake fidda wa. rungume su na yi tare da fashewa da kukan azabar da hannuna yake min, ko matsi nayi da hannun sai naji zafin har cikin raina. Mun jima zaune agurin jin tamkar karamin zafin ake a hankali na lallaɓa da kyar na mike, na kamo Naseem da hannun na mai lafiyar na ɗagoshi da kyar na iya goya shi, dan shi yafi Nasmah jin ciwo. ina matse idanuna hawaye na zuba cikin jin azaba, sannan na ɗauki Nasmah na rike ta a ɓarin hannuna mai lafiyar, gefe na na waiga in da ɗankwali na dana ɗaura musu duwatsun wasan su yafaɗi can gefe shima na isa na ɗau ka da hannuna mai ciwon, Jin wani irin zugi da hannun yayi min sai na sake ɗankwalin kasa, na juya ina faɗin "Naseem Nasmah bazan iya ɗauka muku abun wasan kuba hannuna yana min ciwo idan na samu wasu zan ɗiba muku a hanya". a sannu na soma tafiya ina ɗaga kafata ahankali-ahankali, sai kuma na tsaya a raina nake faɗin "To yanzu idan na tafi na bar ɗankwali na anan a ina zan samu abun da zan ɗaura a kaina idan na cire hijabi na na rufe su Nasmah da shi?". nayiwa kai na tan bayar, idanuna na rumtsa nasan idan na ɗauka hannuna zai min zafi. a raina nake ayyana na kunce Duwatsun na zubdasu sai na ɗauki ɗan kwalina nasan shi bazai min nauyi ba. na koma in da yake na ɗauki ɗan kwalin ina kokarin kuncewa nayi nayi na kunce na kasa saboda da hannu mai ciwon ne jin hakan yana daɗa kara ramin zugin hannuna ne sai na bari. na zaunar da Nasmah a kasa Sannan naɗan kunce zanin goyo na cusa ɗan kwalin sakanin bayana da jikin Naseem,sai na mayar na ɗaura, kana na ɗauki Nasmah muka fara tafiya a hankali. dan yanzu bana iya tafiya da sauri dan duk jikina ciwo yake min ga su Naseem har yanzu suna ta kuka. Idan muka ɗan tafi kaɗan sai na sauke su na huta kana muku ma ci gaba, Abun mamaki munyi tafiya mai nisa amma har lokacin bamu iso in da shanun nan suke ba, daga can saman tudun da muka gangaro da nake hango su banyi zaton zanyi irin wannan tafiya mai ni haka ba kafin na iso su. a haka dai nayi ta tafiya har na iso kusa da su, wasu matasa Fulani ne guda biyu suke kiwon shanun,suna tsaye can gefe sai dai na lura basu san da zuwa na gurin ba duk da dai sakanin mu da ɗan tazara, a sannu na isa gindin wata bishiya na zauna kana na sauke su Naseem, nayita rarrashin su Nasmah har sukayi bacci. muna nan zaune a gurin har yamma sai sannan makiyayan nan suka fara kaɗa shanukan,sunayin gaba, Ganin haka na mike da sauri na ɗauki su Nasmah narika bin bayan su duk inda sukayi ina biye da su,idan suka tsaya na tsaya idan suka cigaba da tafiya nima na bisu. haka dai mukayi ta tafiya har naji badaɗi gashi babu halin nace zan tsaya na huta sutafi su barni, tafiyar nake ina matsar ƙwalla sabo da tsaɓar gajiya gajikina da ya daɗa kara yin tsami, muna nan muna tafiya har guri yafara rufawa. can naga shanun sun tsaya kana a sannu naga sunayin kwana can na hangi bukkoki gefen bukkar cikin wani gurin da a ka zagaye shanun suka shiga, nan makiyayan suka fara ɗaure su, a sannu na karaso gurin sai na tsaya gefe da garken shanun ina ta raba ido, Fulani mazaunan gurin sunata harkokin su wasu daga kusurwa daban-daban suna ta ɗaure shanukan su da alama suma yanzu suka dawo daga kiwo, numfashi na sauke tare da yin murmushi cikin zubda ƙwalla gani na acikin mutane wan da nagama fidda sammanin yiwuwar hakan, a hankali na tako na tsaya kusa da garken shanun.... wani dattijo ne yafito daga cikin wani gidan da ke gefe da garken shanun, kana yashiga cikin shanun cikin girmama wa da ladabi matasan makiyayan nan suka shiga gai dashi cikin girmamawa,ya amsa cikin sakin fuska kana yashiga tayasu ɗaure shanun. jijjiga Naseem da yake ta musu-musu a bayana nashiga yi dan nasan yagaji ko kuma jikin sa ya masa tsami dan yabugu sosai,ina matse ido hawaye na zuba, tuni Nasmah ma ta saki kuka, sai na cigaba da gargiza su ina hawaye, yan da nake girgiza sun hakan yasa hannuna ke girgiza zafi har cikin raina. da sauri dattijon nan yafito daga cikin garken shanu yana ɗan waige-waige da alama dai kukan yaran yaji yasashi fitowa duba da yan da yake ta ɗan waige-waige, nan idanunsa ya sauka kanmu da mamaki yake kallona kana yace "Ke wanene me kike yi a na?". yayi maganar idanunsa a kaina cikin hausar sa da bata tsaya ba, banyi magana ba sai masar ƙwalla nake, "Ke wanene nace me yasa mi yaron?". cikin zubda ƙwalla nace "Munfaɗi ne shine yaji ciwo kuma yunwa suke ji". "Yunwa?". yafaɗa yana kallo na". na gyaɗa kai na alamar Eh, yaɗan yi shiru yana kallona, kana ya kalli su Naseem da Nasmah da kyau sannan yace "Garin yaya kuka faɗi haɗarin mota ne ina zaku je??". yajero min tambayar nace "Acan kan tudu muka faɗi kuma Yola zamu". shiru yakumayi alamar nazari kana yajuya tare da faɗin "Kubiyo ni". ai ko da sauri na bi bayan sa. ya shiga gidan tun daga bakin kofa yake faɗin "Sumaye Sumaye Sumaye". wata yarin yar dake zaune a tsakar gidan ta mike tana faɗin "Inna wuro Bappa na kira". wata dattijo war mata tafito daga cikin bukko da sauri tana amsa kiran sa, tare da faɗin "Gani nan Malam". yace "Zo ga wani bakuwa nan tazo kuma wai yaron ta ya faɗi a kasa kuma yana jin yunwa bashi abinci yaci". tace "Subhanallahi kawo shi nan mugani garin yaya?". namatso in da take tana kokarin karɓar Naseem dake ta zandara ihu, garin cirosa sa a bayana sai ta bige min hannun, yarfe hannun nayi tare da faɗin "Wayyo Allah hannuna". tace "Ayya Allah kam sansu ke ma hannunka na siwo ne?". kai na gyaɗa cikin zubda ƙwalla nace "Eh da muka faɗi ne nima na buga hannuna". kallon yarinyar dake zaune a gefe tayi tace "Zo Mero kikarɓa mata yaron hannun ta". yarin yar ta matso da sauri ta karɓi Nasmah, tace "La Inna wuro itama taji ciwo". Inna wuro tace "Oh wani irin faɗuwa ne haka sai kace haɗarin mota". tafaɗa tana roko hannuna tare da cigaba da faɗin "Ko dai haɗarin mota kukayi ne". yarfe ɗaya hannun nayi nace "Wayyo Allah na". Inna wuro tace "Malam itama ta buga hannun ta inaga tayi targaɗe a hannun". "Nima dai haka nace kamar wan da suka faɗi a mota". yamatso kusa da ni yana faɗin "Naga hannun". naɗago haka na mika masa yarike yana ɗan jujjuyawa, rumtsa idanuna nayi da karfi ina faɗin "Wayyo Allah wayyo Allah". yace "Sannu kinyi targaɗe ne". sai ya saki hannun "Bari nakawo magani nasha maku". Bappa yafaɗa yana shigewa cikin bukko, ni dai yarfe hannun narika yi ina matsar ƙwalla. yana shiga yafito da wasu robobin mai guda biyu, ya dawo in da nake. Inna wuro tayi sauri ta ɗauko taburma ta shin fiɗa tace na zauna, na zauna shiko a kan kujera ƴar tsuguno ya zauna kana yaruko hannuna yaja yaja yajijjiga shi da ɗan karfi, kara na sake cikin jin azaba har cikin kokon zuciya ta, ina shushshure kafafu kasa kamar zan saki fitsari a jikina. kana yabuɗe ɗaya daga cikin roban mai daya fito da su ya lakato maganin ciki yashafa min a hannun da tuni yahaɗa zufa,kana ya saki hannun yana yimin sannu. Inna wuro tace "Sannu zakiji daɗi har kiyi bacci". kai kawai na gyaɗa mata ina matsar ƙwalla, na matsa baya na jingina da jikin garu ina rike da hannun da ɗaya hannuna... ya karɓi Naseem yashafa masa maganin dake cikin ɗaya robar a duk kanin ciwukan jikin sa, yana yi yana ɗan mammatsa jikin sa har ya gangaro kasan kafar sa ai ko yana rike guiwar kafar sa yakara sautin kukan sa yana kankame jikin sa, kafar yarike da kyau yaja sai ga kafar tayi kass, Maganin da yashafa min a hannu yashafa masa a kafar yana faɗin "Gocewar kashi ne". kana ya mikawa Inna wuro shi ta karɓe shi tana girgiza shi da yi masa sannu, nan ya karɓi Nasmah itama ya sha fa mata bayan yagama dudduba jikin ta ko itama da buguwa ko gocewar kashin a jikin ta,sai dai ita ba a samu gocewar kashin ba sai dai buguwar kawai... Ina zaune nayi jugum zuwa lokacin kam alhamdllh zafi da zugin da hannuna yake min sai raguwa yake, ido na zubawa su Naseem da ke jikin Inna wuro sunyi shiru sunata rarraba ido, Bappa kuwa tun da yagama shafa mana maginin yamike yafiya sai yanzu yashigo rike da kwarya a hannunsa, ya karaso in da muke ya mikawa Inna wuro kwaryar yana faɗin "Basu susha dan su daɗa jin karfin jikin su". Inna wuro ta amsa tare da faɗin "Dama yanzu nake shirin aiken Mero taje ta tatso musu madarar". ta aje kwaryar ta mike da sauri ta shiga bokkar dake gefe da mu tafito da kwarya da ludayi guda biyu, ta raba madarar biyu ta mika min rabi kana ta zauna tana ɗibawa da ludayi tana baiwa su Naseem, ai ko suka karɓa suna ta sha, A hankali na ɗibo nadarar cikin lodayi nakai bakina, lumshe idanuna nayi jin ɗumi da garɗin madarar ya ratsa ni,ai ko na gyara zamata sai gashi na shanye madarar tass har ina tanɗe baki... Bappa ya fito da shirin tafiya masallaci ya dube ni yana faɗin "To ni zan tafi masallaci yanzu ina zakuje tun da naga kun gama shan madarar?". kaina a kasa nace "Yola zanje". suka haɗa baki da Inna wuro wajen faɗar. "Yola??". Bappa yace "To ke da zakije Yola me ya kawo ki rugan nan Yola da yake tacan gefe Yola da yake tacan mezai sa kibiyo ta nan?". ko mai ban ce ba sai kasa da kai na da nayi. da sauri ya juya yanufi kofa yana faɗin "Bari na tafi kar na rasa sallah". a hankali na mike nace "Ni ma zan yi sallar". Mero ta mike da sauri ta zubo min ruwa a buta ta mika min tare da nuna min banɗaki. na je nayi sarki kana nafito nayi al'wala, koda na fito na samu Inna wuro ta shinfiɗa min sallaya Mero kuma na rike da Nasmah sai wasa da gashin kanta daya cukuikuye take, bayan na idar da sallar ina zaune kan taburma tuni su Naseem sun yi bacci,sai na gyara musu kwanciya kan taburman na rufe su da abun goyon su. Mero da Inna wuro ma duk lokacin sun shiga yin sallah.. ina zaune jigum... Bappa ya shigo da sallama, na amsa kallon in da su Naseem suke kwance yayi kana yace "A'a ya zaki kwantar da yara a wannan gurin sanyin ke bakyajin sanyi?". murya ya ɗagaga yashiga kiran Mero, da sauri Mero ta fito yace "Kira Sumaye tazo ta ɗaga yaran nan anan ya za'a barsu cikin sanyi". da sauri Inna wuro tafito tana faɗin "Ai kwanciya sukayi ne". ta dube ni tana cigaba da faɗin "Ke ma in kin gama ki taso a sanyin nan". ta ɗauke su ta kaisu ɗaki. numfashi na sauke wai yau mu ake ce wa mutashi a cikin sanyi kar sanyi ya kamamu Allah sarki rayuwa bayan acikin ta mukayi rayuwar wata biyu da ɗori.. A sannu na mike nabi bayan su muka shiga cikin bukka. abakin gado gado irin na Fulanuka in da aka kwantar da su Nasmah na zauna. tace idan ina jin bacci na gyara na kwanta a gefen su,a hankali kuwa na gyara dan kuwa baccin nake ji... Washegari da safe bayan mun karya da lafiyayyen tuwon gari miyar ɗanyen kuka wan da yaji man shanu, muka kara da kunu. Bappa ya shigo da madara acikin kwarya mai ɗumi ya bawa Inna wuro yace ta bawa su Nasmah, guri ya samu a gefe ya zauna kana ya dube ni sannan yace "To yanzu kam gari ya waye bakuwa idan kika fita zaki sami motar tafiya Yola dan daga nan babu wani nisan kirki sosai". Kai na akasa na amsa da to, mikewa yayi yashiga bukkan sa ya fito da robar maganin da jiya ya shafa mana, ya dawo ya zauna yaɗau ki Naseem yana shafa mishi maganin a guraren da yaji ciwo yace "Amma kam dai haɗarin mota ne wannan sai yau na daɗa ganin raunukan ashe da yawa ko ɓarayi kuka haɗu da su a hanya suka yi muku duka haka,dan yanzu ɓarayi rashin imanin su gaba yake har yara ma basu bari ba". ƙwalla naji ya cika min ido tuno da yadda akayi muka ji ciwon, cikin zubda ƙwalla nace "A'a ba hatsari ko dukan ɓarayi bane faɗowa mukayi daga kan wani tudu". da mamaki Inna wuro tace "Ikon Allah garin yaya?". Bappa yaɗan sakai ta shafa masa maganin yana faɗin "Garin yaya a ina kuka sami tudu ku da kuke mota ba tafiyar kafa ba kuma kince ba haɗari bane". nace "Eh acan cikin daji acan ta wani guri da nisa zamu zan sauka a kan tudun shine na zame shi kuma ya suɓuce a hannnuna ya gungura yafaɗi kasa ita kuma tana bayana tare da ita muka isa kasa shine na faɗo a kan hannuna". gaba ɗayan su suka zuba min ido alamun na zartata da kuma magana ta kana Bappa yace "Menene yakai ku cikin daji da har kuka kai ga jin rauni??". kasa nayi da kai na ina wasa da ƴan yatsu na yayin da gudun hawaye na suka tsananta cikin rawar murya da kuka ke son kwace min. a hankali nafara basu labarin rayuwa ta tun daga farko har yau da nake zaune a gaban su. Salati Inna wuro ta sake gaba ɗaya jikin ta yagama yin sanyi har sai da taɗiga ƙwalla cike da tausaya wa rayuwar mu, Bakin zanin ta takai tashare ɗan guntun kwallar da ya fito mata tana faɗin "Ikon Allah lallai kinga rayuwa rayuwar ki abun a duba ne, me kika tsare wa mutanen nan da zasu jefaki cikin wannan mawuyacin hali, har ya shafi yaran da basusan kansu ba bare susan mecece duniyar, wannan wani irin zalunci ne". Inna wuro ta karashe maganar tana jan hanci. Bappa kuwa kai ya jinjina cike da dattako sannan yace "Allah mai girma da ɗaukaka, lallai Allah shi ke kare ba wansa a duk inda yake, yatsare ku yakuma kare ku da sharrin namomin daji masu cutarwa har kuka fito batare da cutar wan wani dabba ba,". shiru Bappa yayi tare da zuba min ido na ɗan wani lokaci zuwa can kuma sai ya girgiza kan sa sannan yace "Mutane dai ko da yaushe burinsu su zalunci ɗan uwan su ko ribar me zasu ci da yin hakan?." yayi maganar yana mike wa, da sauri Inna wuro ta ɗago tana duban sa, in da buta yake yanufa yasun kuya yasoma al'wala yana idar wa ya mike, yashige bukkar sa. numfashi Inna wuro ta sauke, tare da mai da duban ta kaina tace "Allah ya tabbatar da alkhairi". Amin nace batare da sanin inda batun nata ya dosa ba. bayan Bappa nabi na kallo ganin yayi al'wala kuma lokacin sallah baiyi ba... Muna nan zaune can yafito rike da jarbi a hannunsa bakinsa na motsi alamun lazumi yake, in da yatashi ɗazu yadawo ya zauna, numfashi yaja ya sauke tare da yin gyaran murya sannan yasoma magana "Hakika asiri akayi miki mummunar asiri ma kuwa, wanda ya sa akayi asirin da wanda ya ai kata sihirin babu imani azuciyar su, bakin sihiri ne mai matukar duhun gaske, rashin imanin wan da ya ai kata abun yakai yakawo, dan kuwa asirin ba zai taɓa karyewa ba har sai shi bokon da yayi asirin ya muku, mutuwar sa shine lakanin karyewar asirin, tabbas wan nan yacika mugu mara imani, babu kuma wan da yasan ranar mutuwar wani sai Allah, Allah Ya takai ta ma dan basuso abun ya tsaya iya haka ba, yana ai ki da babaken aljanu marasa imani, sunso kiyi gaba can da nisa basuso kitsaya iya nan ba, sai dai sun mance Allah baya bacci duk kuma wan da ya dogara da shi baya taɓewa addu'a kuma makarin mumini sam addu'a bata faɗuwa kasa, da yar dar uban giji bazakiyi gaba ba kamar yan da suka so, zamu gwada musu karfin ayar ALHAH!". cikin matukar mamaki da kaɗuwa nake kallon Bappa to wacece Ni da har wani zaiyi min asiri, ni dai nasan anyi min kazafin da har na mutu bazan taɓa mancewa da shiba, to wacece ni da har wani zai nimi yin asiri a kai na. "Innalillahiwa'inna'ilaihirraji'un". nafurta daga zuci har kan laɓɓana. Inna wuro ma salati ta saka tana faɗin "Ikon Allah lallai mutum abun tsoro ne Allah ka shiga saka nin nagari da mugu"... sun jinjina lamarin sosai tare da tausaya min kwarai da gaske...★ Tun daga wannan ranar bacci na yadawo rabi, dan kuwa daga zaran dare ya tsala Bappa zai cewa Inna wuro tata tashe ni yace nayi al'wala nayi salla, yakuma bani Kur'ani nayi ta karatu har sai asuba tayi idan nayi sallar asuba sai na kwan, nan ne zan yi bacci mai tsawo. A ɓangaren sa kuwa shima babu dare ba rana kullum zaka gansa cikin yin Sallah da karatun Alqur'ani, Bappa babban malami ne kuma limami acikin ɗan rugar tasu,yana da ɗalibai magidan ta da yake koyar da su kullum duk bayan sallar asuba, sai ya zamana da yanzu ya kara musu lokutan darasi bayan sallar isha zasu yi da asuba ma suyi. zuwa wannan lokacin targaɗen hannuna ya warke. da duk raurukan jikin mu dan kullum Bappa sai ya shafa mana magani. ★★★★ *After 3 month* ★★★★ Zaune muke a bakin gado bayan Inna wuro tayi musu wanka ina shafawa Naseem mai Mero na gefe tana yiwa Nasmah kwalliya da kayan kwalliyar ta sai dariya nake musu ganin yan da take ta zana mata fuska da kwalli irin kwalliyar su na Fulani. ina gama shafa masa na mike na ɗauko kayan su guda ɗayan nan wanda dashi mukayi ta rayuwa a daji, kullum idan na sa musu idan yayi datti sai na cire musu na wanke,yagama koɗewa har ba a iya gane kalar kayan saboda yayi fari wani gun ma duk ya yayyage. shekaran jiya Bappa ya siya musu yadi irin na Fulanuka yaba da a ɗin ka musu, yace idan aka ɗin ka musu wancan ɗin na dai na sa musu waɗan nan kayan sun mutu. na mikawa Mero kayan Nasmah nace "Gashi idan kika gama mata kwalliyar sai ki sa mata". tace "To adda HAMDAH ba Bappa yace a daina sa musu waɗan nan kayan ya tsufa ba". nace "Eh to ai ba a amso na gun ɗinkin bane shi yasa zan sa musu wannan ɗin". tace "To bari na gama mata kwalliyar sai na goye ta muje gun telan mu karɓo". Nace to. sallama Bappa yayi daga can waje, Naseem najin muryar sa yakama salle yana mika hannu, dan yanzu sun saba sosai dan ko masallaci zai je yarika kuka kenan sai yaje da shi, in ko zaije duba shanukan sa sun dawo daga kiwo sai ya ɗauke shi sutafi tare. in ko Bappa na waje ya ɗan jima bai shigo gida ba sai yaɗau hanyar kofar gida dan yanzu tafiyar sa ta ya fara kwari. ganin yana ta tsalle yana nuna kofa da yin kwalaɓe yana faɗin "Pappa Pappa". sai nayi murmushi ganin karfi da yaji yana son yayi magana, Inna wuro dake bakin kofa tayi dariya da faɗin "Yana kiran mutumin shi ɗaga murya da karfi bai jika ba". nace "Ai kam gashi nan sai tsalle yake kamar zai tashi sama". Mero tace "Yi sauri Adda ki gama sa mishi kayan sai na kai shi". nace to, hannuna na kika ta baya na janyo wandon sa sai na haɗo da ɗankwalina dana ɗaura musu duwatsun nan aciki, ina ɗago ɗankwalin sai guda ɗaya yafita ya faɗi, na ɗauka na sa masa a hannunsa ina faɗin "Ungo abun wasan ka kaje gurin Bappa sai kun dawo Mero kai shi". nafaɗa ina mika mata shi bayan na sa masa wandon, ta karɓe shi tafita ta kaiwa Bappa shi, ya karɓe shi yana faɗin "Mutumin zamuje gurin shanu ko". yayi dariya tare da yin gwalaɓen shi yana tsalle a hannun Bappa. har sunkai bakin kofa zasu fita dutse ɗin da ke rike a hannun Naseem yafaɗi kasa, ai ko yashiga zillewa yana kokarin zamowa kasa, Bappa yagyara rukon sa tare da kallon kasa jin abun yaɗan bigi kafar sa yana faɗin "Tsaya na ɗauko maka abun naka kar.." cak ya haɗiye maganar nasa cikin matukar ɗinbin mamaki yake kallon abun kamar a mafarki, hannunsa na rawa ya mika yaɗauko dutse ɗin, shiko Naseem hannu ya mika yana kokarin karɓar abun wasan sa yana washe baki. cikin tsananin mamaki da kaɗuwa Bappa ke kallon dutse ɗin, kana murya na rawa hatta hannunsa rawa yake yace "Waya baka wannan abun a ina ka samu!". yafaɗa yana kallon yaron da mamaki yake juya dutse'n a hannunsa wan da hakan yake tabbatar masa da ba mafarki yake ba. kwaɗawa Inna wuro kira yashiga yi yana faɗin "Sumaye Sumaye Sumaye". da sauri Inna wuro ta fito tana faɗin "Na'am Malam". dutse ɗin ya ɗago yana faɗin "Wannan abun a'ina yafito daga ina yafito a hannun wannan yaron nagani!". naganar yake cikin kaɗuwa. Inna wuro ta matso gurun Bappa tana faɗin "Wani abun kuma?". tafaɗa tana leko hannunsa yace "Wannan abun daga ina yafito". tace "Bansan ta in da yafito ba a'ina ka ganshi?". tayi maganar ita ma cikin girgiza da ganin dutse'n da yake nuna mata. Bappa yace "A hannun wannan yaron nagani". Inna wuro ta saki kabbara da karfi tana faɗin "Malam ta ya akayi abun nan yashigo cikin gidan nan". Bappa har jikin sa na cirawa yafara kwaɗa min kira yana faɗin "HAMDAH HAMDAH HAMDAH". da sauri na karasa fitowa daga ɗaki dan dama fitar zanyi da naji Inna wuro ta saki kabbara da karfi a tare muka fito da Mero har muna rige-rige. dutse ɗin yaɗago yana nuna min yace "Ta ina yaron nan yasa mo wannan abun a hannun sa nagani". kasan cewar rana yafito dutse ɗin yafafa walkiya har yana kashe ido. murmushi nayi ina faɗin "La wannan ai abun wasan su ne". Ido Bappa ya waro cikin ɗin bin tarin mamaki da shiga shok yace "Abun wasan su!!??" yafaɗa cikin kakkausar murya. kai na gyaɗa ina faɗin "Eh abun wasan su ne na bashi yayi wasa da shi". baya Bappa yayi cikin tarin mamaki yace "Abun wasa? wannan abun shine abun wasa kinsan meye wannan kuwa!?". kafaɗa na ɗaga nace "Oho ni ban san shi ba kawai dai na ɗiba musu ne acan in da muka zauna na ɗiba musu sunayin wasa da shi, to da zamu tafi shine na ɗibo musu naga suna son wasa da shi." baki da hanci Bappa da Inna wuro suka buɗe suna kallona,cike da ɗinbin mamaki kana Bappa yace "Wannan suke wasa da shi? da ahi sukeyin wasa!". yayi maganar yana juya dutse ɗin a a hannunsa. "Bappa to ai akwai wasu ma da yawa na ɗibo musu bari ma kagani". nafada tare da juyawa da sauri nasgige ɗaki, na kunce ɗankwalin na ɗibo guda 9 a hannuna na kulle ɗan kwalin da sauran biyu a ciki na fito da sauri. ina faɗin "Kagan su Bappa". baya Bappa yaja da sauri tare da jinginuwa da jikin garu yana bina da wani irin kallo mai cike da al'ajab tsorone a'a mamaki ne. ni kai na sai da naɗan razana tare da kallon duwatsun hannuna ko ganin yaga wani abun ne ni dai ban ga komai ba sune dai duwatsun a hannuna. Inna wuro ma kirji ta dafe tare da waro ido tace "A ina kika sami wannan abun!?". Bappa kam kasa magana yayi yana cigaba da bina da kallon mamaki. nace "Wlh acan in da muka zauna kusa da ruwan nan na samu acikin wani ruwan da muke yin wan ka shine na ɗiba musu shine suke yin wasa da shi". sai yanzu Bappa ya buɗe baki da kabbara "Allahu Akbar Allahu Akbar Allahu Akbar!". yayi ta nanata kalmar har sau uku kana ya mika hannu yakarɓi sauran na hannuna yana juyasu a cikin hannun shi. ya dubeni da kyau kana yace "kinsan meye wannan?". kai na girgiza nace "A'a". "Allah mai girma da ɗaukaka". Bappa ya faɗa tare da kuma cigaba da faɗin "A wani ruwa kika same su tayaya a kayi kika same su idan mukaje zaki gane ruwan??". yajero min tambayar. na gyaɗa kai na nace "Eh zan gane ai a bakin ruwan mukafi daɗe wa ma". nan nabasu labarin lokacin da ruwan yacika kogin ya mamaye ko ina bayan wucewar sa muka dawo gurin zaman mu da yan da akayi har nasa mi duwatsun. cikin matukar mamaki suka haɗa baki wajen faɗar "Ikon Allah Allah buwayi gagara misali". Bappa yace "Wannan dutse da kike gani kuma kike masa kallon abun wasa dukiya ne arziki ne, kwalli ɗayan sa ma kaɗai ya ishe ki rayuwar duniya ingantacciya mai tsafta, hakika Allah yayi miki ni'imar da bakowa yake masa ba sai wan da yaso". kallonsu kawai nake taya za'ayi ace dutse shine kuɗi nace "Bappa baka gansu da kyau bane fararen duwatsu ne fa". dun kule su yayi a hannunsa gamgam yace "Da ma tun zamanin iyaye da kakanni sunsha faɗan cewa acikin yankin nan akwai arziki muna da arziki sai dai arzikin sai mai rabo yake iya ganin sa har ya same sa,tabbas kun tabbata ke da ƴaƴan ki ku masu rabo ne, wannan duwatsun da kike gane sune *LU'ULU'U*.......!!!!!!!!!★ Mommyn Twins ce 🌺HAMDAH🌺 t NA *RASHEEDA S DIRECTOR* _BOOK TWO_ *Sakon ta'aziyya gareki Aysha Aliyu Garkuwa* *Tabbas babu abun da yakai rashin hamaifiya zafi da kunci😭 Allah yajikan Mahaifiyar ki yayi mata rahama ya gafarta mata yasa Aljanna ce makomar ta da sauran namu iyayen baki ɗaya😭 ku da tabari ya baku hakurin rashi ya sanya albarka a rayuwar ku da zakuyi shi bayan rashin UWA!!*. *Sannu Aunty Aysha rashin mahaifiya akwai zafi Allah yabaku ikon cin jarabawar da yayi muku*😭👏🏻 " *LU'ULU'U?*" nafaɗa ina duban Bappa da mamaki kana nace "Bappa Diamond ƙenan fa?". yace "Eh shine kwarai shine wannan". kai na jinjina cike da matukar mamaki, tabbas naji a na faɗan Lu'ulu'u amma ban taɓa ganin sa ba ko a hoto ne bansan ya kalar sa yake ba, kuma tun da nake tunanin abun bai taɓa zuwa min ƙwaƙwalwa ta bare har na ƙiyasta kamannin sa acikin zuciya ta ba, ni dai naji ana faɗar sunan sa Diamond wato Lu'ulu'u,sai dai kaman ninsa kam sam ban sani ba. baki na washe tare da mika hannu ina faɗin "La ashe dama wannan shine Diamond ɗin da ake faɗar nan ashe akwai a Nigeria ma? in sake ganin su Bappa." nafaɗa ina kokarin karɓa a hannun sa. da sauri Bappa ya daɗa dun kule su a hannunsa yana faɗin "To ai gashi kin gani ai mu arzikin da Allah yayi mana a Nigeria ma wata kasar bata samu kwatankwacin irin sa ba, ke zaki bada shaidar haka tun da gashi kin samo da hannun ki, wannan ba abun wasa bane barsu a hannuna kawai". baki na washe nace "Ashe Diamond ɗin haka yake". Gefe da gefen sa Bappa ya kalla tare da like kofar gida kana ya juyo ya dubi Inna wuro yace "Da muke maganar nan Allah sa dai ba wanda yake kusa ko kin ki motsi alamar mutum a kusa?". ɗan shiru Inna wuro tayi alamun nazari kana tace "A'a kam banji alamun wani a kusa ba". Kai Bappa ya jinjina sannan ya dube ni yace "Kikace zaki gane ruwan idan muka je?". nace "Eh zan gane". da sauri ya juya yashige bokkan sa yayi musu kyakkyawar ɓuya kana yafito, ya dubi Inna wuro da muke tsaye har lokacin yace Kada ta kuskura tafita kuma kada tabar wani ya shigo gidan. tace To,kana ta ja hannun Naseem da Nasmah suka zauna kan taburman dake sakar gidan,tana ta jan su da wasa har muka fita basu sani ba... Muna fita yakira wo waɗannan matasan da suke yi masa kiwon suka taho da amalanken shanu Bappa yace nahau. kana ya dube Ni yace "Ta'ina zamubi?". nan nashi kwatanta musu hanyar da muka bi ranar da na biyo shanun muka shigo cikin rugar. ina kan amalanken su suna tafiya a kasa nan muka ɗau hanya. mukayi ta tafiya tafiya mai nisa kafin muka iso in da na sami shanun suke kiwo, koda muka iso gurin, sauka nayi nan nashiga waige-waige abun mamaki hanyar ta ɓace min na tsaya shiru ina ta kalle-kallen gurin amma kwata-kwata na kasa gane hanyar, ko wannan babban tudun da muka faɗo a kan tama ban ganshi a gurin ba nayi ta waige-waige amma babu ko a lamar sa. "Kodai ba nan bane". nayi maganar a kasan raina. Bappa da tun ɗazu yazuba min ido sai yanzu yayi magana "Kin tabbata tanan ne hanyar?". kai na gyaɗa alamar Eh. yadubi matasan da muka taho da su, tare da kiran sunan ɗaya daga cikin su yace "Isa Kunzo kiwo a nan wace rana kuma?". suka ce masa Eh suka kuma faɗa masa ranar, kuma ranar da nabi su muka shiga cikin rugar su, duk da kuwa basusan ina biye da su ɗin ba. Bappa ya jinjina kai kana ya mai da duban sa gare ni yace "Ta'ina ne gurin?". ɗan shiru nayi tare da lumshe idanuna a hankali suffar gurin duk da bawai mance sa nayi ba yashiga zuwa min idona, na buɗe ido da sauri. nace "Gurin akwai dutse babba sannan a gefen dutse ɗin akwai bishiyoyi karkashin bishiyoyin kuma yashine, gaban su can kuma babban ruwa ne kafin wannan babban ruwan kuma akwai wani fuwa ɗan karami ne sosai". shiru Bappa yayi kana yace "Haka ruwan yake". nace "Eh". ya tan baye su Isa ko sun san wani gurin ruwa mai irin yanayin da na siffanta?, suka ce Eh sun san wani ruwa mai dutse da bishiyoyi. Nan muka juya zuwa wannan ruwan da suka ce sun sanin. Muna zuwa gurin na tsaya na kalli gurin gashi nan shima dai babban ruwa ne amma sam bai kai wan da muka zauna a gefen sa ba, Kuma shima akwai dutse da bishiyoyin amma ba irin wancan ba. nace ba shi bane. Bappa yace muje wani guri shima ya san wani ruwa irin wan da na siffanta, muna zuwa can ɗin ma na kalli ruwa nace bashi bane. ranar munyi yawo mun wuni muna yawo muna zuwa gurin ruwa daban-daban duk wani ruwan da muka je ko kaɗan bai kai girman wanda muka zauna a gefen sa ba daga wan da bai kai shi girma ba sai wanda shi kwata-kwata ma baya tafiya a guri guda yake. Abun mamaki nayi-nayi na tuna hanyar da nabi har mukaje wannan gurin ruwan nakasa gashi dai ina ganin ruwan da duk wani abun da ke gurin ruwan a ido na amma sam na kasa tuno hanyar gurin. duk inda nayi tunanin ta nan ne idan muka je sai naga ba gurin bane, daga karshe muka je gurin wani katon ruwa mai girman gaske girman sa yakusa kai wancan ruwan yanayin ruwan yana kusan shigen kama da wancan amma shi babu dutse da bishiyoyi da wani alamun gurin da muka zauna agurin babu shi. Bappa yayi shiru yana duban katon kogin kana yace "Anya wannan ba shi bane?". nace "Allah Bappa ba shi bane wancan ruwan yafi wannan girma kuma wannan babu dutse da bishiyoyi". yace "To ai shima ga dutse tacan". yanuna gefen mu tacan da ɗan tara saka nin mu, nace "Shi wancan dutse ɗin ba a tagurin yake ba". Shiru Bappa yayi kana daga bisa Ni yace muko ma gida. Washegari ma muka kuma fita niman wannan ruwan sai dai yau tacan makotan rugan su Bappa mukayi, a cewar sa ko tacan ne ruwan yake kai na yakife nake ganin kamar ta in da muka je jiyane. shima har yamma muna yawo babu alamar sa, kwana uku muka jera muna fita, ranar na ukun da yamma muka dawo gida a galabaice muka zube a tsakar gida bisa taburma... Bappa yayi tagu mi lokaci zuwa lokaci sai yace "Allahu Akbar Allah mai girma". Inna wuro tace "Kwarai kuwa buwayi gagara misali". yace "Kwarai kuwa Sumaye Allah buwayi ne gagara misali, tabbas maganar tun zamanin iyaye da kakanni ya tabbata, tabbas maganar su na cewa a kwai arziki a yankin nan kuma sai mai rabo yake iya ganin sa har ya same sa ya tabbata ya tabbata sai mai rabon,ita kaɗai take da rabon gani da kuma samu". Bappa yakuma faɗin "Allah mai girma taya kika gani ne cikin babban ruwan kika shiga kika samu?". nace "A'a Bappa a dai cikin wannan karamin ruwa da ke kusa da babban da na faɗa maka muke wanka da sha da Sallah da shi ɗin, aciki na samu bayan da ruwan ya cika kogin har gurin da muke zaman nan". nan nakuma basu labari kamar yadda nabasu da fari da lokacin da naso tafiya na barshi a gurin da kuma faɗuwar da mukayi naso kuncesu na zubar da su na ɗauki ɗan kwali na. "Ikon Allah wannan abu naki ne shi yasa bai baki ikon zubar da su ba, yayi ta sa miki da ke da ƴaƴan ki son abun a ranku duk da baki san menene shi ba, in da baki da rabo da ko ganin suma bazakiyi ba,idan yaga dama kuma sai ya nuna miki yakuma nufeki da barin su agirin ɗin"... Adaren ranar Bappa yakira babban ɗan sa Mahmud, Mahmoud costom ne yana da zama a Abuja, matar sa ɗaya da ƴaƴansu uku. nan Bappa ya shige bukkar sa dan acewar maganan sirri ne. bayan sun gama magana da Mahmoud yafito nan yake faɗa mana "Gobe idan Allah yakai mu Mahmoud zai zo zai yi hanyar da za'ayi a canza Lu'ulu'u zuwa kuɗi,kuma yace dole sai an haɗa da manyan shuwagabannin Nigeria, tun da har yawan su yakai guda goma, sannan kuma barin Lu'ulu'u a cikin gida tare da mu yana da mugun haɗari, domin kuwa har idan labarin yafita zamu iya fuskantar matsala, dan kuwa ba shakka za'a iya kawo mana hari, gobe da sassafe yace zai taso dan ma yanzu dare yayi ne". washegari da rana Mahmud ya iso rugar, yayi mamaki da jinjina lamarin ta yadda nayi nasamo Diamond masu yawa irin haka, yayi murna da godiya wa Allah da samun wannan ɗinbin dukiyar,yakuma ji daɗin da abun ya shigo acikin gidan su, dan kuwa ba shakka hakan abun alfahari ne. bayan ya huta yaci abinci,zaune muke a tsakar gida Bappa da Mahmoud suna zaune kan taburma guda yayin da ni da Inna wuro Mero Nasmah muke zaune kan taburma guda, Naseem kam na can kan kafar Bappa ya like masa sai tsalle yake a jikin sa. ina zaune shiru duk maganar da Mahmud da Bappa su ke da tsare-tsaren da Mahmud yake na yan da lamarin zai tafi cikin sauki, ban iya cewa komai jikina yayi sanyi natuno wani sashi a rayuwa ta, tun isowar Mahmud da yayi sallama cikin gidan inadaga ɗaki sai da naji gaban kirjina ya yabuga, jikina sai ya kama ɓari muryar sa tamkar muryar Abba har na fara tunanin ko Abba ne sai da naji Mero tana faɗin Oyoyo Yaya Mahmoud. ko yanzu da muke zaune ganin fuskar sa shima ya sani shiga wata yanayin, kamannin sa irin na Abba yana matukar kama da Abba. sai dai shi baikai Abba girma ba shekarun sa bazai wuce 38 zuwa 40 ba, kira ce tashigo wayar sa da sauri ya ɗaga kiran kana yakara wayar a kunnen sa "Ok godiya nake". abun da yafaɗa kenan tare da sauke wayar. maganar sa naji a sama yana faɗin "Tun jiya na nimi ganawa da gwamnatin jihar nan, gashi da ikon Allah cikin sauki an bani tabbacin ganawa da shi cikin sauki in sha Allah, wa gwamnati za'a siyar domin samun cigaban kasa". ya mike tsaye yana cigaba da faɗin "Bappa mu hanzar ta." tun kan ya rufa baki Bappa yamike yana faɗin "masha Allah hakan yayi". bukkar sa yashiga zuwa can yafito yana gyara babbar rigar da yasa ka kan kayan jikin sa,tuni Mahmud yayi waje Bappa na fita ya shige mota suka ɗau hanya... kwance nake a kan gado Nasmah da Naseem suna gefe na sai wasa suke,Mero ta shigo nace ta ɗauke su sufita dan kaina ciwo yake min sai kuma dami na da surutun su suke, suna fita na gyara kwanciya ta,gaba ɗaya yau tunanin gida da ya dame ni tun ganin da nayiwa Mahmoud tunanin family na ya addabe ni,ina kwance shiru a haka har bacci ya ɗauke ni... Bappa sun isa cikin Adamawa batare da ɓata lokaci ba suka sami ganawa da Gwamnan jihar su, saboda muhimmin abun da ke tafe da su. bayan sun gabatar da abin da ke tafe dasu, shi kansa Gwamnan yayi mamakin yawan Diamond ɗin, yace gaskiya wannan Daimond ɗin kam sai dai a jingina da shugaban kasa. sabo da babu kuɗin da zai iya canza wannan Diamond ɗin a fadar jahar. batare da ɓata lokaci ba yayi magana da fadar shugaban kasar Nigeria, kana ya haɗa su da wasu jagororin da zasu tafi tare, sannan yace dole sai sun tafi da wanda yasamo Diamond ɗin sabo da za'a iya bukatar hakan acan fadar shugaban kasar. da yamma lis suka baro cikin Adamawa suka koma rugarsu da jagororin da aka haɗa su da su, da sojoji mota guda waɗan da zasuyi musu rakiya, dan acewar gwamnar komawar su cikin daji da wannan abu yana da haɗari sosai dole sai an haɗasu da jami'an tsaro. mota uku ne motar Mahmoud sai na jagororin da aka haɗa su dasu motar su guda sai motar sojojin. motar su Mahmoud ne a gaba na jogororin a tsakiya na sojojin na biye da su... bayan sallar Isha muna zaune a tsakar gida muka jiyo jiniyar sojoji, Ido Inna wuro ta waro tare da faɗin, "Sojoji kuma shanun wa aka kuma kaɗawa yau?". batakai ga rufe bakin taba muka ji jiniyar ya tsaya daf kofar ida, Mero tace "Inna wuro anan suka tsaya". tafaɗa tana nuna kofar gida, ganin yan da sukabi suka tsorata nima sai na fara shiga yanayin da suke ciki, har kuma lokacin jiniyar na tashi, nace "Eh..Eh akofar gida suke". duk mukayi jigum idanun mu a kofar gida tsoro fal zuciyoyin mu. bayan haka dakamar minti 15 muka jiyo sallamar su Bappa duk muka mike tsaye tare da amsa sallamar. suka karaso ciki,tun kan su zauna Inna wuro tace "Malam lafiya da sojoji a kofar gida?". ganin duk hankulan mu a tashe yasa Bappa faɗin "Babu komai fa rakomu sukayi domin su bamu tsaro sabo da abun da muke tare da shi". tsaguwar sa ya gyara kana yace "Duk ku zauna". nan muka ɗan sami kwarin guiwa muka koma mazau nin mu, Mahmoud yacewa Mero ta tashi tazuba ruwa acikin bototi, tana zubawa ta mika masa yakarɓa yafita,yakai wa ba'in da suke tare da su a waje. Bappa ya zauna kan taburman sa da Inna wuro ke shinfiɗa masa duk dare a bakin kofar sa kana a nutse yashiga faɗa mana yan da sukayi da gwamna kana ya ɗaura da faɗin "Sai ki shirya tun yau dan gobe idan Allah ya kai mu da sassafe zamu tafi". kai na gyaɗa cike da mamakin jin abun da Bappa ya faɗa. Inna wuro tace "Ikon Allah to Allah ya kai mu sai ki tashi ki kimsa". to kawai nace dan ni ban san me zan kimsan ba, ba kaya nake da shi ba bare na ce shi zan kimsan, su Naseem ma ba kayan suke dashi ba sai kala bibbiyun da Bappa ya ɗin kamusu. washegari da sassafe Inna wuro ta tasheni,tace naje nayi wanka taɗaga su Nasmah taje tayi musu wanka, ta shirya su, ina fita ta bani wani kayan ta mai ɗan haske na saka duk da kayan yaɗan min girma, Mahmud yashigo yace nayi sauri ni ake jira, da sauri na karasa saka hijabi wan da shima ita ta bani, Inna wuro da Mero suka rako ni har waje,tuni kowa ya shige mota sojojin nan suna saman motar su sun tasa bindigogin su gaba, da hannu Mahmud yayi min alama da inzo, na karaso gun motar sa na buɗe gidan baya muka shiga ni da Nasmah, Naseem kam tun da yaga Bappa yarika mika hannu yana tsalle Bappa yace a kawo shi.. motar sojojin a gaba yayin da motar mu ke biye da shi sai na jagororin a baya.. nan muka ɗauki hanyar birnin tarayya Abuja....★ muna isa garin Abuja wani kayataccen masauki aka wuce da mu, nan Mahmoud ke faɗa wa Bappa, an tabadar da masaukin domin mu ne, ɗakina ni da su Nasmah da ban, ɗakin Bappa da ban sai na Mahmoud ɗin,sai kuma na jagororin da muka taho da su, sojojin kam suna cin abinci suka juya suka ɗau hanyar Adamawa,dan da ma suma rakiyar sukayi mana yanzu kuma kulawar mu yafita a hannunsu yadawo hannun wasu hukumar da muka tarar da su a nan. a gayiye na zauna bakin gado Naseem da Nasmah suna zaune tsakiyar gadon sunata wasan su. bin lafiyayy ɗakin nayi da kallo, numfashi na sauke ashe dai zan sake gani na cikin ɗaki irin wannan, dan ni na fidda sammanin hakan arayuwa ta mai cike da tarin kaddara da jarabta. kasan cewar mun isa ana kirana sallar magriba, dan da muka iso sai da muka tsaya a wani guri naga jagororin da aka haɗo mu da su, suka tsaya yin magana da wasu, mun ɓata lokaci a gurin kafin muka taho nan. kayan jikina na tuɓe na ɗaura zanin a kirji nashige bathroom naje nayi wanka,sannan na fito na tuɓe su Naseem suma naje na musu, ina fita na shinfiɗa sallaya da nagani cikin ɗakin kasan cewar nayi al'wala nagabatar da sallar magrima. tuni su Nasmah sunyi bacci sabo da gajiyar mota, sai na gyara musu kwanciyar su a kan lafiyayyen gadon, bayan na idar da sallar Isha ina zaune a kan sallaya akayi knocking ɗin kofar, a sannu na mike na isa bakin kofar na buɗe, wani mutum nagani sanye da uniform irin na masu ai kin hotel, da tray ɗin abinci a hannunsa, yayi min sannu na amsa,baya mayi na ɗan ja murfin kofar ya shigo ya dire tray'n kan table ɗin da ke tsakiyar ɗakin mai lodin kayan abin ci da drinks kala-kala kana yafita, na mai da kofar na rufe, na koma bakin gado na zauna. da ma yunwa na ke ji nan na janyo tray'n na soma cin abincin, inaci ina kallon su Naseem dan na san suma yunwar suke ji sai dai gajiya ya sasu bacci, ina gama ci naje na wanko bakina na dawo, na kwanta bakin gadon tare da yi musu addu'a nima nayi nagyara kwanciya ta. washegari bayan nayi wanka nayiwa su Nasmah na shirya su muna zaune,a ka shigo mana da breakfast bayan mun karya. Bappa yashigo da sallama kan kujerar ɗakin ya zauna, nan nashiga gaida shi ya amsa kana yake tanbaya ta ya gajiyar hanya?, nace "gajiya yabi jiki". Naseem kuwa tuni ya wuce jikin sa yana ta tsalle Nasmah ma tabi bayan sa sunata yi masa gwalaɓe,suna ta shekewa da dariya Bappa shima sai biye musu yake yana ta taya su sai zuba masa surutu suke wan da ma maganar tasu bagane ta ake ba. zama Bappa yagyara tare da duba na kana yace "Ɗazun Mahmoud ya zo ya same ni da jagororin da aka haɗa mu da su sun bani tabbacin bazamu sami ganin shugaban kasa a yauba, zamu ɗan ɗau lokaci sai dai kawai muɗan jira, idan kuma zamu koma to,amma gaskiya ni ina tunanin komawar mu domin iyanzu maganar Lu'ulu'u'n nan ya karaɗe cikin rugar mu har da wajen sa, ina tunanin mukoma yanzu mutane basa da gaskiya ɗai-ɗai ku ne masu gaskiya a zamanin yanzu, yan da yashiga kunnen mutanen gari kuwa na tabbata zai fita har wajen gari, har miyagon mutane suje suji sukawo mana farmaki, gaskiya bazamu koma ba zamu jira har lokacin da zamu sami ganawa da shi shugaban kasar". kai na jinjina alamun gamsuwa tabbas, kuɗi a gida akwai haɗari musamman irin wannan da na ga gwamna yahaɗo mu da jami'an tsaro, nace "To Bappa duk abun da ka yanke dai-dai ne". yace "Gaskiya zamu zauna ko nan da kwana uku ko huɗu ne in dai har zamu gana da shi ɗin yafi mana komawar mu da dukiya kan hanya domin ko a hanyar komawar mu ma kaɗai hatsari ne bane kuma ace mun koma cikin ruga in da babu jami'an tsaro". nace "Hakane Bappa muzaunan kawai". kai ya jinjina kana ya mike yana rike da hannun Naseem, Nasmah da take ta kokarin binsu yace ta zauna ta tayani hira, zai tafi da Naseem shima ya tayashi hira.... kwaman mu uku a Abuja acikin wannan hotel ɗin, alhamdllh a kwana na ukun bukatar mu ta isa ga shugaban kasa sai dai har lokacin ba'a bamu da mar ganin sa ba, a kwana na biyar,da safe ina zaune akayi knocking naje na buɗe kofar Mahmoud ne yashigo da sallama, rike da babban laida a hannunsa, na gaishesa cikin girmamawa ya amsa tare da mika min laidar dake hannunsa tare da faɗin "Gashi ku shirya kuyi sauri, yau kam in sha Allah zamu sami ganawa da shi koba shi ɗin bama zamu zauna da wasu manya na kusa da shi kuyi sauri ku shiriya ya zama na dai da kuna cikin shiri". nace "Tom". na karɓi laidar tare da yi masa godiya yafita. na zawo bakin gado na zauna tare da buɗe laidar na fara ciro kayan cikin, kayane na sawa,kaya masu kyau narika ɗaga na Naseem da Nasmah masu kyau ƴarkanti, dukan su da takalmar su masu kyau, da ma tuni na riga da na musu wanka, na cire musu kayan jikin su nasa musu wannan kayan, yara suka fito shar da su tamkar ƴaƴan turawa, sunyi kyau sosai na tasasu gaba inata kallon su cikin ban sha'awa, sannan nima na mike na camza nawa dogon riga ne da gyalen sa Ash mai ratsin gold ɗin duwatsu haɗe da takalmi Black and gold, takalmin mai ɗan tudu ne kaɗan. nasaka kayan a hankali na isa yaban mirror abun da na daɗe banyi shi ba yau nayi, nashafa pawda da nagani kan mirror'n haɗe da man lips kana, nayi rolling ɗin gyalen a kaina,tsayuwa ta na gyara gaban mirror'n masha Allah duk da na rame na dishe amma bai hanani fitowa a HAMDAH ta ta daba kaɗan ba, murmushi nayi ganin yan da nayi kyau a cikin kayan yaɗan ɓoye min rama ta. da misalin karfe 12 Mahmoud yashigo daga bakin kofa yatsaya yace nayi sauri na zo. sai ya juya yafita , cikin hanzari na sakawa su Nasmah takallamar su sannan na kama hannunsu muka fito, muna fita farfajiyar hotel ɗin, nan na tadda su, Bappa yana zaune cikin mota gefen mai zaman bamza yayin da Mahmoud ke zaune a mazaunin direba. muka karaso Bappa yana ta kallon mu yana murmushi, nima murmushin nayi muka karaso na buɗe gidan baya na shiga Naseem kam fir yaki shiga sai da na mika sa wa Bappa. motar mutanen da mukazo da su a gaba namu yana biye da shi a haka muka fita a cikin hotel ɗin, duk san da na ɗago kaina sai mun haka ido da Mahmoud,na lura tun fitowar mu idanun sa a kaina, kawar da kaina nayi gefe ganin sai satar kallo na yake tacikin mirror, munyi tafiya mai nisa kafin muka isa wani katon gida mai matukar girma da kyau da tsaruwa, a bakin get ɗin gidan motar gaban mu ya faka a bakin get ɗin Mahmoud ma ya tsaya a bayan sa, ɗaya daga cikin mutanen ya fito ya isa in da sojoji ke zaune a bakin get ɗin, yayi magana da su kana ya koma cikin motar, nam sojojin suka buɗe get ɗin, motar ta fara shiga kafin mu muka bi bayan sa. sai da na shiga gidan na daɗa ganin tsaruwa da girman sa, muka paka a parking lot. kana mutanen suka fito daga cikin motar,ɗaya daga cikin su yazo yace, muma mu sauko. daga can wasu sojoji suka taho in da muke,jogororin da muka taho da su suna gaba muna biye da su muka nufi cikin gidan, yayin da sojoji biyu ke gaban mu. wani lafiyayyen parlour muka bayyana cikin sa,nan da nan aka cike mu da kayan ciye-ciye da na sha. munkai kimanin awa ɗaya zuwa can mukaji takun sauka daga step's a hankali na ɗago kaina wani mutum ne ya karaso cikin parlour'n cikin girmamawa gaba ɗaya ƴan cikin parlour'n suka mike tsaye, a sannu ya karatsa ya zauna kan wani kujera lafiyayye,nan kowa ya zube yana mika gaisuwa, nima dai ɗan tutsunawa nayi na gaishe sa, ɗan shiru ne yabiyo bayan gaishe-gaishe sannan mutumin yayi gyaran mursa sannan yace "Sannun ku da zuwa kune ba'in ko?". waɗan da muka zo da su suka amsa da Eh. waya ya ɗaga ya daddanna sannan ya kara a kunnen sa, yayi magana zuwa can ya sauke wayar, kana ya mike yadubi su Bappa yace su biyo shi,suka mike da waɗan da mukazo da su ɗin da sojojin da suke tsaye har lokacin a cikin parlour'n suka fita,suka bar ni ni da su Nasmah a cikin parlour'n. tun da suka fita har akayi sallar azahar ina nan zaune har wajen karfe biyu da rabi, babban damuwa ta ma sallar da banyi ba. can wani soja ya shigo yayi min magana cikin harshen turanci yace na biyo shi, na mike na ruko hannun su Nasmah muka bi bayan shi. muna fita wani mota ya nuna min na shiga, direba na zaune cikin motar shikuma ya zauna mazaunin mai zaman banza, nan direba yaja motar muka fita a gidan. tafiya muka yitayi har na fara tsorata da tafiyar,naɗan ji tsoro ganin dukkamsu ban san suba, ganin mu nayi bakin wani ramɓasheshen get mai girman gaske, aka buɗe mana get ɗin muka shiga shima tafiya mai tsawo mukayi a cikin wannan get ɗin kafin muka kuma isowa wata get ɗin, nan mukayi ta wuce get-get kuma ko wanne da sojoji. wata get muka iso mai kyau da tsaruwa muka tsaya nan kira yashigo wayar sojan, ya ɗaga bayan ya sauke wayan ya dube ni yace na sauko. nafito jiki a sanyaye, tafiyar kafa mukayi mai tsawo, kafin nan muka iso wani kofa, Hmm in da ranka ka sha kallo tsaruwar wannan guri bazai misaltuba, sojoji ne a tsaye a gun duk kanin su foskokin su sanye da bakin glass, nan suka shiga saka mana na'ura a jikin mu suna gwada mu,ni da su Naseem,kafin muka haura kan step ɗin da zata sada mu da kofar, nan kofar ma, tafara bada wani sauti tana ɗaukar hotunan mu,abun mamaki da al'ajabi, daga bisa ni kofar ta buɗe muka shiga, sojan na gaba ina biye da shi a hankali, koda muka kuma isowa wata kofar nan sojan ya tsaya wani sojan da ke tsaye nan bakin kofar shi yayi gaba, yayi min alama da na biyo shi, koda muka kuma zuwa wani kofar ma, tsayuwa wannan sojan yayi kana sojan da ke tsaye a wannan bakin kofar yayi gaba da ni. muna zuwa wata kofar mai shigen, kama dana farko yakuma ɗaukar mu a hota,ina tsaye ina kallon ikon Allah abun dai ya fara bani tsoro, shima still anan sojan ya tsaya sojan dake wannan bakin kofar yayi ciki. "Innalillahi ya ilahi ya lillahi". abun da na furta kenan, wani mashahuriyar katon parlour ne kamar ba a duniya yake ba, wannan parlour'n muka shiga yanuna min gurin zama na zauna. sai na janyo ƴaƴana na rungume su dan nasan sun gama gajiya da wannan tafiyar, munyi zaman da yakai na 30min, kafin daga can wata kofa ta buɗe wani mutum yafito yayi min alama da nazo na mike nabi bayan sa, nan muka kuma shiga wani gurin na daban wan da yafi ko ina girma da tsaruwa. muna shiga gurin can da nisa na hango su Bappa zaune kan wasu tsararrun kujeru, numfashi na sauke, cikin tsananin mamaki da kaɗuwa nake kallon wan da yake zaune kan kuje ran dake gaban su Bappa, da mamaki nake lallon mutumin, shugaban kasar mu na Nigeria ke zaune gaban su Bappa na karaso in da suke na zauna a kasa har lokacin mamakin ganin sa fal zuciya ta, mutumin da nake ganin sa a TV da mujallu,sai kuma cikin ɓarin baki nashiga gai da shi. cikin sakin fuska fuska ɗauke da annuri ya amsa gaisuwar, kai Bappa ya ɗan dukar cikin ladabi da girmama wan da yariga da yafi ka cikin girmama shugaba yace "Ranka shi daɗe wannan itace yarin yar". yafaɗa yana nuna ni. annurin fuskar sa ya faɗaɗa idanun sa a kai na, ya jinjina kansa. hannu ya miko yayi wa su Naseem alama da suzo, ai ko Naseem sarkin sabo ya mike ganin ya mike sai Nasmah itama ta bi bayan sa, hannun su ya ruko yana faɗin "Masha Allah sannun ku jarumai". yafaɗa yana shafa kawunan su. baki suka washe kamar sun san abun da yafaɗa shima yabisu da murmushi haɗe da yi musu wasa... bayan wasu maganganun da yayi da na kusa da shi, wan da duk kanin mu babu wanda yaji abun da suke faɗa, kana ya mike yabita wata kofa. ɗaya daga cikin mutanen da suke zaune a gefen sa yadube mu yace wa wasu da ke gefen mu a tsaye sukai mu masauki. nan muka mike muka bi bayan su wani masauki na musamman a ka kai mu, nan ma kowa da ɗakin sa. anan muka kwana ɗaya washegari da safe aka buga min kofa koda na buɗe breakfast a ka shigo da shi wan da ya kawon cikin harahen turanci yace min na hanzarta mushirya a kwai kaya acikin ɗakin muyi amfani da su, nace to. na ɗaga su Nasmah na basu abinci nima na ci, sannan mukayi wanka ,muka kimsa cikin kayan da naganau cikin wardrobe ɗin ɗakin lafiyayyun kaya na manya da yara. muna gama shirin akayi knocking na kofar koda na buɗe wasu mutane ne maza guda biyu sukace min muje, To. nace sannan na koma cikin ɗakin na kamo hannun su Nasmah mukabi bayan mutanen. acan waje muka haɗu da su Bappa nan muka shige mota mukayi gaba. ido nazubawa hanya a raina nake faɗin "Yau kuma ina za'a yi da mu?"....★ tundaga bakin get ɗin da yanzu muka iso na fahimci airport muka zo a bakin get ɗin muka haɗu da Mahmoud, muna isa tuni sojoji sukayi ciki da mu. direct in da jirgi yake suka nufa da mu, lumshe idanuna nayi tare da kuma buɗe wa lokacin da na ɗaura kafata kan step ɗin jirgin, sai nake ganin komai tamkar a mafarki. "To ina kuma yanzu za'ayi da mu a cikin jirgi?". nayiwa kai na tambayar......!★ Ayi hakuri da typing error busy over👌🏻 *Wlh na fiku matsuwan ganin na kammala littafin nan hausawa sukace in aski yazo gaban goshi yafi zafi insha Allahu mun kusan isa.*🤦🏻‍♀️ *Ina barar addu'ar ku wacce tagoye ni tamkar mahaifiya aguna Allah yayi mata rasu*😭😭😭😭 Mommyn Twins ce A sannu narika taka matattakalar jirgin, har muka shige ciki, Kujerar da ke kusa da window wani mutum ya nuna min yace na zauna anan. kana ya ɗago su Nasmah da Naseem ya ɗaurasu kan kujerar da ke gefe na, ya janyo sit belt ya sarkafe su da shi. tun shigar mu cikin jirgin hankalin jamar cikin da ma'aikatan jirgin duk yadawo kaina, sai nuna ni suke suna magana wan da ni bajin me suke faɗa nake ba, sai dai yanzu na fara tsarguwa da yawan kallo da nuna ni da mutanen suke. ina zaune shiru sai raba ido nake a cikin jirgin, Allah mai iko wai yau nice gani a cikin jirgi wan da da sai dai na hangosa daga nesa in muka yiwa su Abbu rakiya in zasu tafi Saudi. sai gashi yau gani a cikin sa ko ina za'a kuma kai mu yau oho, ina kuma za'ayi da mu acikin jirgi?. Kamar Bappa yasan abun da nake ta sakawa cikin zuciya ta,ya mike daga kan kujerar da yake yatoho in da nake, da ƙagan sa kasan yana cikin matsanancin farin ciki, bashi kaɗai ba hatta Mahmoud tun ɗazu bakin su yakasa rufuwa, yakaraso in da nake cikin matukar farin cikin da yagama mamaye ilahirin zuciyar sa Yace "HAMDAH Allah yayi miki albarka Allah yadaɗa karawa rayuwar ki albarka, hakika rayuwar ki mai cike da ɗinbin albarka ne, yau gashi ta sana diyyar ki zamu tafi kasa mai sarki". Amin nace cikin rashin fahimtar in da maganar Bappa yadosa, "Kasa mai sarki?". nayi maganar da fuskar tambaya da kuma rashin fahimta. da sauri Bappa ya gyaɗa kansa kana yace "Eh kasa mai sarki zamuje Saudi zamu tafi yau da yardar Allah, domin kuwa shugaban kasa yace can zamuje a canza yagama duk wani abun da yakama ta duk wani abun da ya dace adalin shugaba nagari ya gudanar da shi, zamuje can a can zamuje a canza, do min yace a can za'a fi canza shi da farashi da daraja mai kima a can sunfi mu sanin daraja da kimar Lu'ulu'u, bugu da kari kuma yace a nan babu isasshen kuɗin da zai canza waɗan nan Lu'ulu'u'n duka, dan a yanzu tsaron kasa ya sa a gaba, Shi yasa yayi magana da masarautar Saudiyya can za a kai musu su zasu canza insha'allahu, Allah dai yayi miki albarka yakarawa rayuwar ki albarka da ke da ƴaƴan ki baki ɗaya". Bappa yarika zabgamin addu'a da samin albarka. Mahmoud daga can yana zaune sai washe baki yake, Ido na waro tare da furta "Bappa Saudi fa Saudiyya zamuje yanzu?". nayi maganar cikin muryar dariya mai bayyana matukar farin ciki, Bappa kam kai yashiga gyaɗa wa yana faɗin "In sha Allahu". Wani irin matsanancin farin ciki ne ya lulluɓe ni wai nice zanje Saudi nice a jirgi da zai kaini Saudi. har lokacin Bappa na tsaye yanata zabgamin addu'a da sanya albarka har sai da ma'aikatan jirgin suka ce yazo ya zauna lokacin tashi yayi. nan ne ya koma mazaunin sa. Nan na'ura tafara bada sanarwar jirgi zai tashi kowa ya kimsa. duban Naseem da Nasmah nayi tare da gyara musu zaman su murmushi nayi ina faɗin "Nasmah Naseem kunsan in da zamuje kuwa yara makka zamu". nafaɗa ina dariya suma baki suka washe. Batare da ɓata lokaci ba jirgi ya ɗaga da mu, cikin yardar Allah da buwayar sa. Idanuna na lumshe tare da kuma buɗe wa ina yiwa Ubangiji buwayi gagara misali godiya, lokacin da na ganmu muna keta hazo, tabbas Allah mabuwayi ne kuma mai izza, sai baza idanuna nake cikin gajimare ina kallon wasu da ke cikin jirgin har sun sami da mar yin bacci, ni kam zunzurutun farin ciki da murna ko ɗigon bacci bana jin sa a cikin idona.....★ Da misalin ƙarfe 3:15 jirgin mu yasauka a kasar Saudi wayyo Allah, zo kuga farin ciki da murna bakina kasa rufuwa yayi daga Ni har su Bappa bakin ko wannen mu a buɗe yake. bayan saukar jirgin da kamar minti 15 nan aka umurci fasinjoji da su sauka, bayan murfin jirgin ta buɗe da kanta. A hankali na mike ina kokarin cire belt ɗin jikin su Nasmah, da sauri wani ya iso in da muke cikin hanzari yayi abun da nake shirin yi tare da ɗaukar Naseem, daga can wani shima ya karaso da sauri ya ɗauki Nasmah kana sukayi gaba nikuma na bisu a baya. su Bappa suna gaban mu, tunkan mukarasa sauka daga saman matattakalar jirgin sojojin kasar Saudi suka buɗe murfin motacin su da ke pake a cikin airport ɗin. Lumsh idanuna nayi lokacin da na sauke fafafuna kan kasar Saudi tare da yiwa Ubangiji tasbihi, a ɓangaren su Bappa ma haka abin yake Bappa kam har sai da ya ɗaga hannunsa sama yanayiwa Ubangiji da ya halicci wannan sarkakakkiyar kasar godiya da ya nufesa da zuwa cikin sa. daga can sojojin kasar saudi sanye da uniform ɗin su, suna tsaye jikin motocin su, tun kan mukarasa sauka sukayi hanzarin nufo in da muke, Nan suka samu a gaba mu da jagororin da shugaban kasar mu yahaɗo mu dasu, sauran sojojin da ke tsaye jikin motar sukayi hanzarin buɗe mana mota, muna karaso wa muka shige ciki, yayin da Ni Bappa Mahmoud Naseem Naseem, muke mota guda sauran motocin kuma jagororin mu suka shige ciki. batare da ɓata lokaci ba sukaja motar mukayi gaba, Ido nayi ta bazawa kan shahararren titin da muke tafiya kansa da kayatattun guraren da muketa wucewa, Kai jama'a na rantse babu kasar da takai Saudi kyau duk tafiye-tafiyen ka duk wani yawon buɗe idon ka zuwa wasu kasashe daban-daban har in bakaje Saudi ba, to Tabbas bakayi kallo ba, baka kuma baiwa idanunka abinci mai kyau ba..... Wani kayataccen masauki aka sauke mu, bayan munci munsha munyi su wanka, Bappa yace muje masallaci muyi sallah, wasu sojoji uku sukayi mana rakiya zuwa Masallaci sai bayan sallar isha muka dawo masaukin mu a gajiye dan munyi sallole kam ba iyaka, tun a cikin masallaci su Naseem sukayi bacci, a cikin parlour sojojin suka dire su saman kujera, ɗaukar Nasmah nayi na nufi ɗakin da a ka sauke ni ɗazu, shin fiɗa Nasmah da ke hannuna nayi kan lafiyayyen gadon, da ɗan sauri na juyo jin an turo kofa, Mahmoud ne rike da Naseem, gefe na ja tare da soma cirewa Nasmah takalmin kafarta, ya karaso bakin gadon ya shin fiɗa shi, Ina ɗagowa muka haɗa ido da shi, saurin kawar da kaina nayi,na lura tun a mota yake ta satar kallo na sai ya rika niman yimin magana musamman idan muna hira da Bappa sai ya rika saba ki ciki, yana fara sa baki cikin maganar ni kuma zanyi shiru haka kawai nake jin mogun nauyin sa, gefen sa na bi ina kokarin wuce sa yace "Shima kicire masa takalmin zai masa nauyi ai". yafaɗa tare da nufar kofa yafita, a sannu na isa na cire masa takalmin, zubewa nayi a gefen su dan bacci ne tam ido na.. Washegari bayan mun dawo daga masallaci muka tadda an cike mana parlour da breakfast kalolin abinci iri-iri irin na gida Nigeria da kuma irin na nan kasar Saudi, bayan munci munsha mukayi su wanka, aka kuma ɗiban mu da sojoji jama'a sai gamu a fadar Saudi, Ya ilahi ya lillahi na ga karrama wa naga karamci daga gurin larabawa, gaskiya larabawa akwaisu da karrama wa, nan da nan ina za'a saka akarika yi da mu tamkar mu wasu ne, anawani kafa-kafa da mu. Nan da nan aka cike mu da kayan cime-cime irin na larabawa....★ Bayan maganganun da ya gudana sakanin fadar Saudi da jagororin kasar mu da shugaban kasar mu yahaɗo mu da su, nan fadar ta bukaci ganin Diamond ɗin, nan Bappa ya ciro sa cikin lajuhu wan da suke ɗaure cikin laida ya mikawa ɗaya daga cikin jagororin mu, kana shikuma ya mikawa wani na kusa da shi sannan shi kuma yamika wa da dukkan alamu hukuma ne, ya karɓa kana ya taka zuwa sakiyar katafaren parlour'n saman table ɗin dake gaban wani farin dattijon balarabe yana zaune cikin kamala da dattako fuskarsa ɗauke da annuri, ya aje laidar, tare da yin magana cikin harshen larabci. shugaban shima yayi magana cikin harshen larabci da sauri wani da ke zaune a kasa kusa da kafar sa ya mike ya shinfiɗa wani farin gyalle kan table ɗin kana yashiga kunce laidar, ya juye Lu'ulu'u'n kan farin gyallen. wani dake tsaye taɗan can gefe rike da wani ɗan karamin a kwati ya maso da sauri tare da buɗe ɗan karamin a kwatin, yaciro wani na'ura kana yamaso kusa da table ɗin, ya ɗaura na'urar kan Lu'ulu'u'n nan na'urar ta kawo haske tare da bada ɗan sauti, idanun mutumin tar a kan na'urar, yaɗau mintuna da ɗan dama kana yaɗago, cikin garshen larabci yayiwa wan da nafi tunanin shene shugaban magana, kai ya jinjina tare da duban mu da murmushi ɗauke a kan fuskar sa,kasan cewar bama jin bama jin larabci shima bayajin yaren mu, sai ya juya cikin harshen turanci yake magana, "To a binciken da akayi yanuna wannan asalin *LU'ULU'U* ne muna tayaku murna". yafaɗa fuskarsa ɗauke da yelwataccen murmushi, ai ko gaba ɗaya gurin yakace me da hayaniya kowa yana faɗar albarkacin bakin sa, sai faɗi ake wai wanene yasamo Diamond kuma wai a Nigeria. mutanen saudi suke maganar, nan jagororin mu suka nuna ni, nan aka rika nuna Ni a na faɗin nice nasamo diamond ɗin, sai kawai nadawo abun kallo, sai nuna ni ake wasu kam ma sai sun zo har kusa dani suna tayani murna, wasu cikin harshen larabci suke magana sai dai bana fahimtar su gara waɗan da suke magana cikin harshen turanci suma ɗin dakyar sabo da harshen su yanuna da Larabci turancin nasu da kyar nake iya ganewa. nawo abun kallo har hotuna sukarin ka ɗaukawa dani, wani zaizo kawai yatsaya yaɗauki hoto da ni, mutane suka rika shigowa suka rika kallo na ni da yarana suka rika ɗaukar su Naseem da Nasmah,suka rika magana cikin harshen larabci idan suka juya da turanci ne nake ɗan fahimtar su, sukayi ta yabawa yaran da kokari da gararabba da sukayi a bakin ruwa kafin mu samo Diamond ɗin, hatta shugaban sai da ya jinjina min. nan da nan ya umurta aje banki a kawo kuɗi, muna nan zaune har waɗan da sukaje kawo kuɗin suka dawo aka rika shiga da gana masgo-masgo cike tam-tam da kuɗi, aka tarasu a tsakiyar parlour'n. ido na ware cike da tsananin mamakin ganin yan da ake buɗe gana masgo ɗin ana ciro kuɗi a ciki, kuɗi irin na kasar su. "Sai kace kasa ko kuɗin ganye, to me zamuyi da wannan kuɗin?". nafaɗa a fili har sai da Mahmoud dake kusa da ni yajuyo ya kalleni, wasu larabawa ne suka shigo da sallama,in da shi shugaban yayi maga da harshen da muke ganewa wato turanci yake cewa sune masa na farashin Lu'ulu'u, nan suka ƙiyasta kuɗin Lu'ulu'u'n batare da ɓata lokaci ba. nan da nan aka fara zuba kuɗin cikin na'urorin kirga kuɗi da suka kai guda goma, wan da duk da su akazo daga banki da kuma ma ai katan bankin. bayan an shafi tsawon awanni ana kirga kuɗin masana farashin Lu'ulu'u' sukayi magana da shugaban, kuma umurtar su yayi a koma a karo kuɗin dan basukai kuɗin Lu'ulu'u'n ba, wannan karon har da zinari aka haɗo. aka rika kirga kuɗin duk gana masgon da aka kirga kuɗin cikin sa sai a maida kuɗin ciki a rufe a kuma zubuta a dadin kuɗin cikin sa,haka akayi tayi anayi ana rubutawa. ni dai ido na zubawa sarautar Allah ni ban ma iya kirga tulin gana masgo ɗin da suketa tura kuɗi ciki kamar takardu ba,har naji na gaji tamkar nice na'urar dake kirga kuɗin, da mutanen da suketa sakawa cikin gana masgo ɗin. bayan da aka gama kirga kuɗin a ka jibgesu a sakiyar parlour'n haɗe da gwala-gwalai da sauransu.... Wannan dattijon balaraben da ke bada umurnin duk abun da za'a yi, yayi gyaran murya tare da nuna kuɗin kana yasoma magana cikin harshen turanci, "Wannan shine kuɗin Lu'ulu'u'n". nan kuma ya bukaci a kira masa shugaban kasar Nigeria, cikin hanzari na kusa da shi yaɗaga waya ya danna kiran lambar shugaban kasar Nigeria,kana ya haɗa shi da shi, nan yake sanar masa an ƙiyasta kuɗin Lu'ulu'u'n sannan kuma gashi an kirge shi, nan shugaban kasar mu yabukaci a haɗa shi da Bappa,yace yaya za'ayi da kuɗin, Bappa yace kawai a sashi a sanunun banki dan bamusan yanda zamuyi da wannan kuɗin ba. shugaban kasar mu ya turo da number account ɗin da za'a saka kuɗin ciki. nan shugaban yabada umurnin a tafi da kuɗin banki, nan da nan aka fara fita da kuɗin, a ka kwashe su zuwa banki, a ka zuba su cikin account ɗin da shugaban kasar mu yabada na bankuna daban-daban.....★ masauki a ka kuma mana acikin masarautar, kwanan mu uku a gurin naga halacci iya halacci, nadawo abun kallo har daga waje ana zuwa kallo na duk wan da yazo kuwa sai yayi hoto da ni. har nayi kawaye ƴan matan larabawa ƴan cikin masarauta. idan naji suna larabci sai nace su koya min, nace an ya ma kuwa zan iya?, sai suce zan iya babu wuya.....★ Acan cikin garin Bauchi kuwa, zaune Ya SALEEM da Na'ima suke a parlour'n sa........!★ mommyn Twins ce Suna zaune cikin parlour'n Ya SALEEM, yayin da shi Ya SALEEM ke zaune saman 1str ya tasa system a gaba yana ta faman latsawa, Na'ima ko na kwance saman doguwar kujera, lodin yankakkun Apple da kankana da abarbane cikin plt a kan table ɗin da ke gaban ta, daga kwancen take mika hannu cikin plt ɗin tana ɗibar yankakkin Apple da kankanar tana kaiwa bakin ta, yamusa fuska tayi sannan ta mike daƙyar tana cigaba da yamusa fuskar, sai kuma ta mike da sauri ta nufi toilet dake nan cikin parlour'n, tazubar da yawon da ta tarashi cikin bakin ta kana tajuyo a hankali, ɗagowa Ya SALEEM yayi yana binta da kallo, da kyar take ɗaga kafa, tarike kugu da duka hannayenta tana wani tafiya da kyar, ta dawo gurin zaman ta tana wani yamusa fuska, bin ta da kallo yake har ta zauna , zaman sa yaɗan gyara yakuma duban ta tare da faɗin, "Amai kika kuma?". cike iya kirsa da makirci takuma yamusa fuska kana tace "Banyi amai ba amma dai inajin zuciya ta na tashi sai dai nakasa yin aman sai yawu da yabi ya dame ni". yace "Subhanallah duk kayan zakin da kike ta sha ɗin na bai sa kin dai na jin aman ba?". baki ta yamusa tace "um to dai gashi ni dai ina jin wannan abun da nake tashan bazai sai da min aman da nake jiba". "Oh sannu". yafaɗa ya juya tare da ci gaba da abun da yake. ido ta waro a kanshi ganin ya juya cikin ko in kula da damuwar ta ya cigaba da abun da yake, a kasan ranta take faɗin "Idan boka na kan tudu ya kasa juya wannan bahagon halin naka, zan kaika wa wani bokan ya juya min wannan halin ko ohon naka". cike da kwarewa a makirci ta marairaice fuska cikin shagwaɓe murya tace "Haba My SALEEM iya abun da zakace min kenan,sannu kawai ai yakama ta kayi wani abu nifa wlh wannan cikin yana damu na, ciki da masafaffen laulayi haka, nifa cikin nan yana bani wahala wlh ni kam gara acire shi kawai na huta". tayi maganar ne cikin kirsa da son gano yan da yake jin son cikin a ransa. da sauri ya juyo ya kalleta tare da faɗin "What! azubar fa kikace?". kai ta gyaɗa cikin shagwaɓa tace "Wlh ni wannan cikin yadame ni wai ace duk abun da nace baya min daɗi, duk abun da naci sai na rikajin zuciya ta na tashi ni,babu abun da zanci naji daɗin sa kawai ni dai inaga cire sa shine samun kwanciyar hankali na". da sauri yace "Ke bakida hankali ne zakice azubar, cikin ne za'a zubar Na'ima?". kai ta kawar dan ba haka taso ba, har yanzu takasa gane SALEEM duk asirin ta da makircin ta, har yanzu takasa juyashi yan da take so, yan da taso tarika juya shi yan da take so sai dai har yanzu bata sami damar hakan ba, duk wani makircin ta da surkullen ta kuwa, bata taɓa iya juya SALEEM son ranta. sai dai wani lokacin takan ɗan sami yadda take so daga gurin sa sai dai ba duka yan da take bukata ba. a yanzu takan ɗan sami nuna kuwalar sa a gare ta, uwa uba bukatar sa yanzu baya barin sa a jikin sa, kullum sai ya sauke sa a mararta, hakan ba kara min da ɗi yake mata ba dan yanzu ma da kan sa yake niman ta, akasin da da sai ta nima da kanta. A son ta tana so ya nuna mata kulawa fiye da kulawar da yake nunawa HAMDAH a da, sai dai ina duk yan da taso hakan bai samuba, ko kwatan-kwatan yan da yake nuna kulawa da rawan kafa lokacin da HAMDAH take da ciki, da kafin ma samun cikin, baya yi mata. system ɗin gaban sa yaɗan ture kana yamiko hannunsa yaɗan shafi gefen fuskarta yana faɗin "Sorry da ma ai an ce duk mai ciki haka take ji har fiye ma da hakan, so hakuri kawai zakiyi har Allah yaraba ku lafiya, yanzu kam ma ai kin kusa hutawa tun da yashiga wata huɗu kenan, kinga ko kin ɗau gangarar hutawa tun da an ce wuyan ta ciki yafara kwari ne da zaran yafara girma zaka fara hutawa da laulayi,to kin ga kuwa kin kusa hutawa kenan". rass. taji gaban kirjin ta ya buga shiru ta ɗan yi tare da tafiya cikin tunani a kasan zuciyar ta. sai kuma da sauri tadawo da kallon ta san sa jin yana faɗin "Wannan cikin dai ina ga shine a ke ciwa mai bin jiki,to ina ga shima yabi jikin ki ne gashi dai har watan sa huɗu amma bai fara bayyana ba,wata kila in yafara girma yanuno kansa nan zaki ɗan ji daɗi". hannu ta mika taɗauki yankakken Apple takai bakin ta tana tauna cikin nuna rashin jin daɗin abun da take ci tace "Ni wlh tsabar wahalar da cikin nan yake bani bansan har yashiga wata huɗu ba". tayi maganar yayin da zuciyar ta ke tunano mata lallai wannan watan ne yayi dai-dai da cikin watan sa huɗu kenan. murmushin gefen baki yayi kana ya mai da idanun sa kan wayar sa da ya ɗauka kan hannun kuje rar da yake kai. sannan yace "Ai abu na jikin ki ma kina mance kwanakin sa? tun lokacin da na sami labarin cikin nake lissafin sa". ɗan dimm tayi sai kuma tayi saurin kawar da maganar da faɗin "Wlh ni ina jin kwaɗayin gwaten gauta, ina ga abu mai ɗan ɗaci-ɗaci yafi gyara min baki". "Gwaten gauta kuma to ke meye zakiyi da wani gwaten gauta?". yayi maganar har lau idanun sa nakan wayar sa. tace "Allah ni shi nake jin sha'awar na sha zan dai na jin bakina ba daɗi, kasan fa tun ranar da Raliya tayi ta kawo min na sha ranar na wuni ban zubda yawu ko amai ba,har nakuma ci abinci lafiyar Allah babu jin rashin daɗin nan, gashi yan zu Raliya batanan tayi tafi bansan yaya zanyi ba, bansan wama zai yi min in sha ba." cikin fara gajiya da surutun ta da son sashi yawan magana da take yace "Kiyi da kan ki mana har sai wani yamiki kafin kisha, tun da ciwon bai kwantar da ke ba kina iya tashi mai zai hana kiyi da kan ki, sai a samo miki gautar kiyi ai, ko kuma kisa Rufa'ila tayi miki ko sauran ma'aikatan gidan". yana gama faɗa ya mike tsaye yana rufe system ɗin sa. Ido tawaro tace "Rufa'ila? Rufa'ila'r ce zata yi min girki wlh bazan ci girkin Rufa'ila ba, kawai kasa dai a yimin". takarashe maganar tana bubbuɗe kofofin hanci. da ɗan mamaki yajuyo yakalleta ganin yan da tayi maganar a tsaye kana yace "To wa kike so ya miki ni kike so naje nayi miki? babu masu girki ne a cikin gidan da sai na nemo masu yi miki?". ganin yan da ya sauya fuska sai kuma ta shagwaɓe fuska tana faɗin "A'a kai kuma haba dai kadai sa ayi min dan Allah my SALEEM ina so na sha". "Wa kenan zan sa yayi mikin?". yafaɗa yana kokarin barin gurin. da sauri tace "Dan Allah kayiwa Mamie magana dan nasan ita zatafi iya yin gwaten tun da dai abincin gargajiya ce, ita zatafi yin mai daɗi ma dan Allah kayi mata magana sai tayi min". bai kuma cewa komai ba har ya juya zai bar gurin sai kuma ya ɗago wayar sa ya laluɓo lambar Mamie ya dan na kira. bayan sun gaisa yaɗaura da faɗin "Mamie wai Na'ima ce ke son shan gwaten gauta ko zakiyi mata". daga cikin wayar Mamie tace "Yanzu ma haka shirin fita unguwa nake, tasa ma'aikatan ta suyi mata mana in bazata iya yi da kan taba, kaganni nan fita ma zanyi". Mamie na gama faɗar haka ta kashe wayar. duk abun da suke Na'ima na ji dan wayar a speaker yasa ka, batare da yajuyo ba yace "To kinji abin da Mamie tafaɗa bata nan zata fita so kawai kisa ayi miki". yafaɗa tare da gyara rukon system ɗin sa ya nufi bedroom ɗin sa. wani irin kololon bakin ciki ne ya tirni ke ta, wato koma damuwa baiyi ba, shidai yakan nuna yana son cikin amma irin rawan kafa da yake nunawa lokacin cikin HAMDAH sam bayayi a kan cikin ta. tsaki taja ta tare da mike wa, sai gatanan ta ware tana tafiya normal bakamar irin yanda ɗazu tayi da taje zubda yawo cikin toilet ɗin parlour'n ba. ta nufi side ɗin ta da sauri ta shige ɗakin ta tana shiga, ta ɗau wayar ta takira kawarta Raliya, Raliya na ɗagawa tace "Aminiya ya kike ya gida ya cikin mun dai?". Raliya tayi maganar da dariya dariya duk suka saka kana Na'ima tace "Him kedai bari aminiya ciki yana nan, ke ni ba na mance ba ashe dai cikin yashiga wata huɗu ni bana gama sakarkancewa ba kwata-kwata ni na ma mance da lissafin ashe ɗan batalikan nan yana nan yana rike da lissafin". dariya Raliya ta fashe da shi. tace "Ke da abu ke jikin ki baki rike lissafin sa ba". Na'ima tace "Himm ke dai bari ai ni na wasar da lissafin tun wancan ranar ashe dama haka mukayi lissafin cikin yanzu yake cemin wai cikin wata huɗu kenan yanzu yakusa shiga biyar kenan, to idan yashiga biyar ba'aga ciki yana tashi ba yaya kenan, karfa asiri ya tonu". Raliya tace "Haba dai sai kace ba Na'ima da na sani ba ya kike wani abu kamar ba kece Na'ima ba,ta ya za'ayi ya gane da zaran cikin yakai wata biyar in yaga baigirma ba sai muyi hanyar da zamuyi sai kawai ace ya zuba". "Kwarai kuwa haka za'a yi kawata kin kawo mafita amma bazai taɓa zuba ba sai ya bani miliyan 5 ɗin na yanzu ma zan shirya in ce masa zanje awo ina zuwa kuma zan kira sa in haɗa sa da Dr Hashim Wargi in tsara masa yan da tafiyar zata kuma ci gaba". kuma shekewa da dariya sukayi, Raliya tace "Kai kawata kina fa tsula tsiyar ki". tace "Yan da nake so kuwa in juya acikin gidan yanda naga dama". sai kuma taɗan sassauta maganar tare da cigaba dafaɗin "Amma ki san meye aminiya?". Raliya tace "Sai kin faɗa". tace "Allah yanzu ina son cikin nan da gaske narasa yan da zanyi ne kawai kinsan rannan naje gurin boka nace mishi yasake duba min yagani anya kuwa bazan haihuba, yace min maganar kenan fa ɗaya tas koyayen haihuwa ta na gama da su,wai ashe sauran sa kenan zuwan mu akan mahanar kuɗin da nake so SALEEM ya banin nan, yabaiwa aljani durkus jinin duk cikin da zanyi nan gaba kin san wai ashe bayan dawowar mu da wata biyu nasami ciki banko sani ba aljani durkus da akayi masa sadakar jinin yaɗauke cikin yaje ya shanye jinin, dama wai shike nan ya rage duk na wanke sauran tun muna makaran ta,to ni yanzu abun yafara dami na kin gafa SALEEM yana son haihuwa yana son yara, narasa yadda zanyi kinga fa ta sana diyyar ganin hankalin shi naga yafara komawa kan yara idan abokan sa sukazo da yaran su karkiga yan da yake yi da su, gudun kada ya tunu cikin wancan ɓatacciyar shegiyar yarinyar nan HAMDAH da kuma abun da zata haifa ko ta haifan ko ta mutu da cikin oho mata shiya sa fa na laune nace ina da cikin nan, sabo da kawai hankalin shi yadaɗa dawowa gare ni, yanzu tsohuwar sa ma wai an kira ta dan rainin wayo nace inaso nasa gwaten gauta kinsan me tace? tace wani wai zata fita unguwa to in yi da kai na mana, kiji matan nan lokacin da wannan ɓatacciyar HAMDAH'N take nan kullum ita ke mata girki tasa akawo mata, amma wai yanzu nace inaso nasha gwaten gauta tace wai nayi da kaina,wato ko da ɗanta ya narka min cikin da gaske haka zatace kifaji matar nan". Raliya tace "To ai yanzun ma na gaskiyar ce tun da koshi uban gayyar bai isa ya karyata ko yagane karya bane, kirabu da ita kawai kin san har yanzu sunajin abun aransu sai dai bazasu iya yin komai a kai bane". Na'ima tace "Ah to sumayi mana ai sai dai abun yakashe su a ransu amma zancen suyi magana kam karyansu, SALEEM yarigada ya zama nawa ni kaɗai idan sukayi wasa ma sai na rabasu da shi in ga ta faɗin su". dariya suka saka dukan su Raliya tace "Yi hakuri dai kada ki raba su bassu a haka kawai aje zuwa tun da babu abun da aka rage ki da shi". tace "Kwarai kuwa SALEEM nawane yazamo nawa, amma kinsan maye ne, Raliya inason magana da ke kizo gida muyi ta, Raliya inason ɗa". Raliya tace "Kinason ɗa kuma?". tace "Kwarai kuwa ina son ɗa ɗan da zai zamo da na SALEEM duk da nasan ni bazan taɓa haihuwa ba,amma ina son ɗan da zai zamo na SALEEM kuma a madadin ni nahaife shi magajin SALEEM yashe zaki zo?". Raliya tace "Zan shigo gobe dan yanzu bana ma gari nayiwa wani saurayi na rakiya, yanzu haka ma muna hotel ne da tun ɗazu kika kira ma bazan sami damar ɗagawa ba,nashiga wanka ne ma yanzu shine kiran ki yake shigo wa." Na'ima tace "To shike nan yanzu yaushe zaki dawo". tace "Gobe ko jibi zamu dawo". tace "To Allah yakai mu kida gobe dan Allah tabbas ina son ɗa wan da zai gaji dukiyar SALEEM". Raliya tace "To an gama ina hanya kuwa". nan sukayi sallama. bayan da Na'ima ta sauke wayar daga kunnnen ta zama ta gyara tare da faɗin "SALEEM dole zan samo ɗan da zai zamo naka yakuma gado min dukiyar ka". tayi maganar a fili yayin da take girgiza kanta alamar yar da da duk wani shirin da ta tufkeshi yanzu a ranta.... a ɓangaren Mamie kuwa tun lokacin da sukayi waya da SALEEM tana zaune a ɗakin ta, bawai fita unguwar zatayi kamar yan da tafaɗa mishi ba, tafaɗi hakan ne kawai dan a ranta tanajin bazata iya girkawa Na'ima abun da zataci ba koda ƴaƴan cikin ta sunkai guda goma ne. tana zaune gan ɗeɗiyar mata da ita wai tana laulayin ciki har da niman mai yi mata girki duk da tulin ma'aikatan da ke gidan su. kai Mamie ta girgiza "Wato dan taga lokacin na HAMDAH ni ke mata girki ko, to ai HAMDAH yarin yace karama tana bukatar tai mako". Mamie tayi maganar a can kasan ranta. yayin da take jin Na'ima wata annoba ce acikin rayuwar su sai dai babu yan da suka ɗiba suka iya da ita. Mamie na nan zaune har Abbu yashigo yakaraso ya zauna a bakin gadon da take zaune, ya dube ta cikin kulawa tare da faɗin "Yaya dai Hajiya Maryamu na ganki shiru haka". murmushi tayi kawai tana faɗin "Babu komai". amma acikin kasan ranta tabbas tunanin HAMDAH ce yazo mata. shima kuwa a ɓangaren Abbu haka abun yake dan tun shigowar sa da yaga tanayin ta shima yashiga irin yanayin datake cikin wan da baki baya iya furtashi sai dai yayi ta kona zuciyoyi... a can cikin part ɗin Ummi kuwa zaune take a kan sallaya kamar koda yaushe tana jan jarbi, bayan tagama yiwa ɗiyar tata addu'o'in samun kariyar Allah a duk in da take. Aunty Rafee'at da Aunty Jaleela kasan cewar yau Saturday ne duk suka tattaro da ƴaƴan su sukazo gida wuni, duk suna part ɗin Ummi da ƴaƴan su, suna zaune suna ta tayata hira, Ummi dai na zaune tana jin su wan da rabin hankalin ta ma baya tare da su. Aunty Rafee'at da ke ta danne dan ne cikin wayar ta har tashi gurin adana hotuna, shiru tayi tare da kurawa hoton HAMDAH sai ga hawaye ya cika mata ido kan kace me yafara gangara kan fuskarta, ido Jaleela ta waro ganin Rafee'at na share kwalla tace "Aunty Rafee'at yaya dai?". fuskar wayar ta nuna mata batafe da tayi magana ba, da sauri ta karɓi wayar yayin da itama kwalla suka ciko idon ta,a fili Aunty Jaleela tace "Ko ya take?". tayi maganar cikin rauni da damuwa sosai. "Sai Allah Allah ka kare ta". cewar Aunty Rafee'at, Ummi ma kwallar ce ta cika mata ido dan tasan mahanar kan HAMDAH suke. ganin Ummi tayi shiru da alamun bayyanar damuwa sosai a tare da ita. sai sukayi saurin kawar da zancen da wani hirar da ban... acan cikin garin Yola kuwa Mama mai awara na hango acikin family house ɗin su, wan da matar yayan ta ta kanainaye gidan yazamo nata dole da ƴaƴan ta. tana zaune cikin waɗi ɗan karamin ɗaki karami sosai, acikin ɗakin take zaune da taburman ta. tazuba uban tagumi, tunanin HAMDAH da halin da take ciki yanzu kaɗai take. lokacin da ta iso Yola ɗan kuɗin da tazo dashi a hannunta ta aje cikin ɗaki akabi a ka sace ta nima tayi cigiya sama da kasa ta rasa, kuma su kaɗai ne agidan daga matar yayan ta sai ƴaƴan ta, amma tayi tan bayar duniyar nan sai matan yayan tace ta ɗaura musu sharri, karshe tayi ta mata wulakanci na kin kari, abincin da take bata ma sai ta daina bata, gashi kuɗin da zatayi kuɗin mota ta koma Narkuta babu tunanin HAMDAH duk yabi ya isheta. ganan ta da taje dan ta saida shi ma taje ta samu wasu sunci gonar, duk yan da tayi akan gonar akace sam ba nata bane karshe haka tabarsu da Allah. wannan ɗakin da take zaune aciki ma tun lokacin da tace kuɗin ta ya ɓata matar yayan nata tace tafita mata a gida da kyar dai tasa mu tabarta tacigaba da zama acikin, wan da da ɗakin kiwon kaji ne zuwan tane ta share shi ta shinfiɗa taburman ta take kwana a ciki. tana so tazo Narkuta taga halin da HAMDAH take ciki amma bata da kuɗin mota, naira goma wannan yafi karfin arzikin ta, tayi yawon niman bashi gidajen da ta sani dan ta fara jarin awara a nan ɗin dan tasamu kuɗin motar da zata takoma sai dai bata samu ba, tana zaune ta zuba tagumi yunwa duk ya addabe ta dan rabon ta da cin abin ci tun jiya da daddare yau kuwa ganin har 12 tayi bata samu abun da zata saka cikin bakin taba sai ta zarce da azumi. yaron matar yayan ta yashigo da kwano a hannu babu ko murfi ya dangwara mata kwanon abincin a gaban ta, babu girmamawa sai zallar rashin tarbiyya, yajuya yafita. tuwone tuwon datsa miyar bakar kuka da ko manja babu a cikin sa, tuwon ɗan haka agindin kwano tamkar ɗan yaye za'a baiwa abincin sabar kankantar sa. kallon abincin tayi kawai ta girgiza kai, batare da takuma kallon abincin ba ta mike ta ɗau mayafin ta tafita a gidan, cikin unguwar tasu tashiga can ciki gidan wasu masu kuɗi dake can cikin unguwar tasu tayi, tayi sallama a gidan matan gidan suka amsa tashiga, bayan sun gaisa tace "Dan Allah kan maganar ai kin nan nakuma dawowa ko Allah zaisa na samu, ko shara da wanke-wanke da girkin abinci ko wanki duk wan da na samu zanyi"..........!★ *Kuyi hakuri kwana biyu bana samun lokacin yin editing sai ku karanta da hakuri idan na samu lokaci zan yi editing cikin document* Mommyn Twins ce Mama mai awara tayi maganar cikin nuna jaddada rokon ta, har in zata samu ai kin tarika samun kwabon kashewa da kuma kuɗin motar da zata koma duba HAMDAH yau sati guda kenan take yayon zuwa gidajen masu kuɗin unguwar su,ko zata sami ai ki, wannan gidan da tazo ma,sun mata alkawarin samin ai kinne tun sati ɗaya da ya wuce, shine yau ta kuma zuwa ko zata samu, ko wani irin aiki ne tana jin zata iya har in zata sami kuɗin mota. Matan gidan suka ce mata Eh sun yi shawarwari zasu ɗauke ta ai ki, amma aikin ba ai kin abinci bane. shara da wanke-wanke da kuma wankin kayan su da na kuma ƴaƴan su, dan suna da mai yi musu girkin, tace ta Amin ce zata iya insha Allah,kuma yanzu zata fara in dai akwai wankin yanzu. Nan aka fara fito mata da lodin kayan wanki ɗaki-ɗaki, ɗakunan gidan kaf sai da suka fito da kayan wanki suka jibgeshi tsakar gida, sannan sukace tafara da wanke-wanke da shara kafin tayi wanki, nan Mama mai awara ta tuɓe hijabin ta ta sha ɗan mara da shi, cikin kankanin lokaci tayi wanke-wanke kana taɗa tsintsiya tasoma shara, tana gamawa sannan ta dukufa wanki mai uban yawa. Wankin take tun tanayi da karfin ta har karfinta yafara kare wa, ga azumin da babu suhur yunwan tun jiya da rana, ta kwana da shi takuma wuni da shi. haka dai tayi wankin cikin mawuyacin hali. tana gamawa ta zauna zaman jiran bushewar sa, tana nan har wankin ya bushe, ta ninke tabi ɗaki-ɗaki tana kaiwa, kamar yan da taga an fito da kayan cikin ɗakunan gidan. Wani ɗakin idan ta kai suka duba kayan su gaya mata maganar banza, suke kayan ma bai fita ba. ɗakin ƴanmatan gidan kam da takai wata yarin ya budurwa da ta karɓi kayan tana dubawa watsa mata kayan tayi a jikin ta, cikin gatsali da tsantsar rashin tarbiyya da sangarci irin na ƴaƴan wasu masu kuɗi tace "Wannan kayan ne kin wanke? ke wata irin mata ce wata irin dakikiyar mata ce ke wannan an wanke wannan kawai tsomasa a ruwa kikayi kika ɓata min kaya kawai". kai kawai Mama mai awara ta jinjina, cikin takai cin jin yan da yarin ya karama wacce ta haife ta tajuya wai ita take zaginta, kallon gefen ta tayi mahaiyar ƴar na zaune a gefen su amma tayi kamar bata nan. "Allah shi kyauta". Mama mai awara ta faɗa a fili tare da juyawa tabar gurin. itako budurwar fuska ta yamutsa tare da jan dogon tsaki, tace "Kayan a kasa zaki barmin kenan kiyi tafiyar ki?". tayi maganar cikin rashin sanin darajar na gaba. Mama mai awara batace komai ba ta juyo takwashi kayan ta mika mata, fizge kayan tayi a hannunta tajuya tawuce ciki... Bayan tayi shara da wanke-wanken yamma daf magriba ta takoma gida, kafin ta tafi kuwa sai da sukayi mata jawabin gobe da sassafe zatazo, ko da ta koma gida da tasha ruwa tuwon da matar ƴaƴan ta ta ɗan sakura mata na tun da rana wan da ya wuni abuɗe ma shi tayi buɗa baki da shi. washegari da sassafen tazo ta gidan masu kuɗin bayan tayi wanke-wanken da shara aka kuma jibge mata wanki har da na jiya da ta wanke aciki tayishi...... tun daga ranar kullum Mama mai awara na kan hanyar zuwa yin wannan aikin, cikin kaskanci da wulakanci da rashin daraja ɗan adam, wannan gida basa da daraja babba duk da ta girme musu duka amma basa daraja ta ko dun girman ta, suna yi mata kallon kaskantacciya kullum cikin wulakancin su take a haka dai har tayi wata ɗaya a karkashin su, ranar da tacika wata guda tana yi musu aiki suka ɗauki naira dubu biyu suka bata suka ce shine albashin ta, Mama mai awara ta karɓa har hanunta na ɓari tanata zuba musu godiya. tana komawa gida tahaɗa ƴan kayakin ta tafita sai tasha, tashiga mota zuwa garin Jos tana isa direct Narkuta ta wuce, ko da suka iso a bakin titi aka sauke ta kasan cewar ɗan kuɗin da ke hannunta duk yakare a kuɗin mota da kafa tashiga layin unguwar su direct ta ɗau hanyar gidan Malam Musa. a sakar gida ta iske Zainabu zaune ta yi sallama tashigo, da sauri Zainabu ta mike tana faɗin "Oyoyo Mama mai awara maraba lale barka da zuwa". Mama mai awara ta yelwata murmushin fuskarta tace "Yauwa Zainabu". Zainabu ta kara buɗe taburman da take zaune a kai tare da faɗin "Sannu da hanya ga gurin zama". tazauna gefen taburman nan suka shiga gaisawa kana Zainabu ta mike ta ɗibo mata ruwa mai sanyi cikin randar kasa ta kaso mata. tasha tana cigaba da mata sannu da hanya. bayan ɗan gaishe-gaishe da tanbayar bayan rabuwa, Mama mai awara takuma bin gidan da kallo akaro na ba adadi jin babu wani alamar motsin wani acikin gidan, ganin yan da Mama mai awara take ta raba ido cikin gidan, Zainabu taɗan muskuta tadube ta tare da yin murmushi tace "Um sai kawai kiga ɗiyar ki tabiyo ki, fir taki zama fa wai ita bazata iya zama ba kawai zata biki, HAMDAH kenan ƴar Mama". Ido Mama mai awara ta waro tare da faɗin "Wa ɗin wai HAMDAH to ai ni ita nazo ɗauka". Zainabu tace "A'a ita kuma kika zo ɗauka Mama mai a wara?, to ai HAMDAH kamma tun ran da kika bar nan da kwana biyar tabiki in ban mance ba". wani irin zabura Mama tayi tare da buga kirji tace "Tun tafiya ta da kwana biyar tabar gidan nan to ina taje?". Zainabu tace "Mama kina nufin wai baku tare da ita?". shiru tayi cike da tsananin damuwa a ranta take faɗin "To ko ta koma gurin iyayin ta ne". sai kuma tayi saurin kuma cewa "Ina baza ta koma ba ko dun gudun ta sana diyyar ta Ummi ta tabar gidan Abba'n ta, ina bazata taɓa komawa gida ba". cikin tsananin matukar tashin hankali Mama tace "Ina Zainabu bataje in da nake ba!" ido Zainabu ta waro tare da buga kirji tace "Bataje ba? nan fa ta shirya tace zata biki nace ta hakura ta barki kidawo tun da kince bazaki jima ba tace a'a zata biki kawai, to ina taje?". Zainabu tayi maganar hankali tashe. hankali tashe Mama mai awara ta mike tana faɗin "Bataje ba Zainabu bataje ba". tanufi kofa, Zainabu ma ta mike taɗau mayafin ta tabi bayan ta, duk gidajen da Mama mai awara take tunanin ko HAMDAH zata iya zuwa gidan wato gidajen da suke mutunci da su anan cikin Narkuta. amma duk in da taje sai suce ai su rabon su da ganin ta tun ranar sunan ta. batun tashin hankali gun Mama ba'a magana, tunani tafara tashiga mota taje Bauchi ta tuba ko ta koma can, sai dai bugu da kari batasan gidan su a cikin garin Bauchi ba,ita dai tace mata ita ƴar Bauchi ce amma bata faɗa mata ko awani unguwa take ba,to yanzu idan taje ta ina zata fara neman ta, Bauchi babban gari ne ba karamin gari ba, idan taje ta ina zata fara neman ta.... Ranar Mama mai awara kuka da hawayen ta tayi da shar-shar, tunanin ta bai wuce ina tatafi wani hali take ita da ƴaƴan ta. kwanan Mama uku ta fara shirin komawa dan tana ganin zaman ta anan nauyi take ɗaura musu, duk yan da taso samun kuɗin mota tatafi batare da sunsan bata da shi ba abun yacu tura, karshe dai malam Musa shi ya bata kuɗin motar komawa. a haka ta koma taje ta cigaba da rayuwar kunci da bakin ciki acikin gidan su wacce matar yayan ta ta mallake ita da ƴaƴan ta, kullum tana cikin tunanin HAMDAH da ƴaƴan ta da halin da suke ciki, duk san da tatuna hakan sai ta zubda ƙwalla, sai dai batayi kasa a guiwa wajen yi mata addu'a ba, duk san da zatayi sallah sai ta sanyata cikin addu'o'in ta.....★ wannan kenan Acan kasar saudi kuwa bayan sati uku da canza Diamond ɗin har yanzu muna cikin masarautar Saudi mun zamo tamkar ƴan gida, Bappa yace bazamu koma ba sai munyi aikin hajji da yake dumfaro wa yanzu. wata ranar juma'a bayan mun dawo daga masallaci shugaban kasar mu na Nigeria yakirawo wayar Mahmoud yahaɗa su da Bappa,bayan gaisawar da ya guda na sakanin su shugaban kasar ke magana kan cewa tun ranar da aka tura kuɗin Diamond baikuma jin wani magana ba, shin akwai wanda za'a basa ATM ɗin bankunan da aka zuba kuɗaɗen ciki nan kasa Nigeria kafin su sudawo?. Bappa yace A'a yarike ATM ɗin a gurin sa dan bayida wan da zai iya cewa abashi sai dai bari yayi wa ita yarin yar magana, yaji ta bakin ta ko da abun da zatace kan lamarin bari a nemeta aji ta bakin ta. I na zaune cikin ɗaki ina sakawa su Naseem kaya da yanzu nayi musu wanka, cikin kayan da ɗazu Bappa yabani kuɗi nasiya musu da muke dawowa daga masallaci. nan yake yimin bayanin yan da sukayi da shugaban kasar mu kana ya ɗaura da faɗin "Ko akwai wan da kike ganin za'a bashi kafin mu koman?". nace "A'a Bappa yan da kace ɗin hakan yayi". yace "To madallh shike nan". ya mike yafita.... da daddare duk muna hallare a katafaren parlour'n da yake masaukin mu, muna cin abin cin dare Mahmoud ya dube ni sannan ya nisa yace "Bappa ya faɗa miki yan da sukayi da shugaban kasa ko?". nace "Eh yafa ɗa min". kai ya jinjina tare da faɗin "Ok to yanzu kina so a bar kuɗin cikin account banki surika juyawa ne ko da wani abun da zakiyi da shi?". Bappa yace "Tan bayar da shugaban kasa yayi min ɗazu kenan da nace masa yabar ATM ɗin agurun su, ni ma dai nayi tunanin ko za'a siyi wasu ƴan kaddarori ne in yaso sai abar sauran banki yarika juyawa". baki na washe tare da faɗin "Eh wlh Bapp a siyi wani abu da kuɗin". Mahmoud yace "To me kike so a siyan". hannayena biyu na dafe kumatu na, nayi sama da kwayar idanuna ina ɗan jujjuya su, naɗan yi shuru alamun nazari, sai nakuma washe baki nace "Bappa kasan me nake tunani kuwa". kai ya girgiza tare da yin murmushi ganin yan da nayi maganar, Mahmoud ma sai da ya murmusa. cikin muryar dariya nace "Bappa kuɗin zai kai yasiya mota da gida?". nayi maganar ina rufe fuskata da cigaba da dariyar, Mahmoud yace "Me zai hana shi kai wan har abun da yafi gida da mota ma zai siya, gidaje da motoci ma ba gida da mota kaɗai ba har abun da yafisu ma kuɗin zai siya da shi har yarage". da sauri nace "Yauwa to kawai a siya motoci irin manyan motocin nan wan da suke loda kaya aciki ana kaiwa garurruwa masu nisa ɗinnan, da gidan mai". yace "Gidajen mai dai". nace "To shi da kuma asibiti da masallaci, umm da kuma irin abubuwan sadakatuj'jariyan nan". Bappa yace "Rijiya bishiya masallaci bohul makaranta asibiti,da dai sauran su duk sadakatuj'jariya ne". kai na gyaɗa da sauri nace "Yau wa Eh Bappa". nakarashe maganar cikin muryar dariya, yace "Gaskiya kinyi tunani mai kyau abun da yakama ta ayi kenan". dariya kawai nayi dan ni ban ɗauki maganar da wata girma ba dan ni atunani na mun dai yi sa cikin rahane amma kuɗin bazai iya yin abun da na lissafan nan ba. Mahmoud kuwa kai ya girgiza ganin yanayin yaranta cike taf cikin maganar tawa...... A daren Bappa ya sanar wa shugaban kasar mu abun da nace ina so ayi da kuɗin, shugaban mu ya jinjina lamarin matuka yace nayi tunani dan hakan ma ci gaban kasa Nigeria ne kwari da gaske. za'ayi abun da nace in yaso sauran kuɗin kuma banki sai ta rika juyashi. bayan sun gama maganar Mahmoud yace to shifa gobe idan Allah ya kai mu zai koma bakin ai kinsa. Bappa yace "To Allah yakai mu mukam muna nan sai munyi ai kin hajji tukun, idan kaje karika zuwa duba mahaifiyar ka akai-akai gobe ma zaka kuma kirowo min Isa ya hadamu mukuma yin magana da ita". yace "To ba da muwa Allah yakai mu".... washegari da misalin karfe 11 Mahmoud yabi jirgi zuwa Dubai in da daga can zai shiga wani jirgin zuwa Nigeria... ★★★★ *After 1 year* ★★★★ 🙌🏻🙌🏻🙌🏻🙌🏻🙌🏻🙌🏻😹 *da yar dar Allah anan book 2 yakawo karshe sai mun haɗu a littafi nagaba wato littafi na uku wan da shine zai zamo littafi na karshe da yar dar Allah* *Zazzaɓin gida-gida yafara kyarkyara ta* Mommyn twins ce