🌺 *HAMDAH* 🌺 *WASA FARIN GIRKI!!*✠*NA* *RASHEEDA S DIRECTOR* _(Book 3)_ _(Bismillahirrahmanurrahim.) Alhamdulillah ina yiwa Ubangiji buwayi gagara misali godiya da ya kuma bani iko a karo na uku nakuma dawowa domin kawo muku cigaban labarin HAMDAH ina rokon Allah ya bani ikon kammala shi lafiyaðŸ‘ðŸ»_ (Afwan a karshen book 2 nasaka (After 1 year) I'm so sorry typing ero ne👌ðŸ») Littafin na siyar wa ne ki biya ki karan ta. domin biyan kuÉ—in littafin sai ka-ki tuntuÉ“i wannan number 08034690723 🅿ï¸?1 Bayan wani lokaci. Tuni ai kin hajji ya karato gamasu niyya tuni aka fara shirye-shiryen tafiya ai kin hajji. kan kace me kasar Saudiyya tacika tayi makil da al'ummar Musulmi. yanzu bama samun wani zama kullum muna hanyar zuwa bautar Ubangiji, ba dare ba rana kullum Bappa na tasani gaba wani sa'in tare muke tafiya da su Naseem da Nasmah,wani sa'in kuma na barsu wa Mammaa mahaifiyar Ukhtee kawata da nayi anan cikin masarautar Saudi jika ga Masarautar Saudi. dan tare muke tafiya da Ukhtee ita kuma Mammaa ciwon kafa ke damun ta bana bazata samu daman fita afara aikin hajji da itaba. acewar ta sai an zurfafa ibada sosai kan lokacin Abdul Malik yayan Ukhtee da yake karatu can jami'ar Madina yashigo zai fita da ita guraren ibada a kan keken zama irin na masu ciwon kafa. kasan cewar na yaye su Nasmah kuma suna cin komai gashi sun saba da matar sosai, shi yasa wahalar su ta É—anyi min sauki ko zamu fita ban cika tafiya da suba.... cikin yarda da buwayar Ubangiji aka kamla ai kin hajji na wannan shekaran lafiya.â˜? tuni mahajjata suka fara komawa kasashen su,nan muma muka fara shiri damin ko mawa kasar mu. ana gobe jirgin mu zata É—aga. tun safiyar ranar jama'ar dake cikin masarautar sukayi ta zuwa sallamar mu. duk wan da yazo sai ya nuna baison tafiyar mu wasu ga fuskokin su wasu kuwa sai sun kai ga furtawa. Ukhtee da Mammaa da tun safiyar ranar muke tare da su a side É—in mu, suka tirje wai sam sai dai Bappa ya barni a nan, ai ko nan kowa yace ya barni shi ya tafi bayan wani lokaci sai na koma. ni dai dariya kawai nake binsu da shi, sai dai zuwa yanzu jikina yayi sanyi ganin yan da Ukhtee take kuka. bilhakki ta rungume Nasmah tana faÉ—in bazan tafi ba. Bappa ko ido yake binsu da shi cike da mamakin ganin zunzurutun kauna gun waÉ—an nan larabawan. ana cikin haka kiran Mahmoud ya shigo wayar Bapp. nan yake sanar wa Bappa yasami masaniya daga shugaban kasar mu anfara duk ayyukan dana lissafa kuma bazai É—au wani lokaci ba insha Allah za'a gama, Bappa yayi fatan alheri kana yakashe wayar. koda naji labarin daga bakin Bappa nayi matukar mamaki dan ni har yau ganin abun nake kamar wasa bazai yiwu ba. Bappa ya mai da hankalin sa kan mutanen da suke cikin parlour'n, abun da ya lura shine suna matukar son ba'i musamman wata kabilar, bugu da kari wan da Allah ya É—aukaka a cikin su, babu garin da zai waye wasu daga wasu unguwanni daban-daban wasu kuma daga É—an garuruwan dake gefen gari basu shigo ganina ba, na zamo abun kallo da hira a gurin su, haka zasuyi ta hotuna da ni da su Naseem. numfashi Bappa ya sauke ganin gabaki É—ayan su kalma guda suke nanatawa.. dun dole Bappa ya amsa musu badun yaso ba da sharaÉ—in zasu sako ni a jirgi nan da É—an kwanaki kaÉ—an. ai kuwa ihun murna Ukhtee ta sake ta rungume ni tana sunbata. gaba ki É—aya parlour'n yakaceme da murna... washegari da misalin karfe 4 na asuba jirgin su Bappa ya É—aga suwa kasar mu ta gado wato Nigeriaâ˜?. kafin ya tafi sai da yayi ta min nasihohi da jan hankali mai ratsa jiki.. tun da Bappa ya koma kusan kullum sai munyi waya ta wayar Ukhtee har da su Inna wuro. Alhmdllh bazan ce komai ba game da zamata anan cikin masarautar Saudi batun samin kula da tarairaya ni da Æ´aÆ´ana kuwa ba'a magana... A can kasar Nigeria cikin garin Bauchi state. Na'ima ce da kawar ta Raliya,tafe cikin mota suka É—au hanyar wani asibiti dake nan cikin G.R.A wan da shine Na'imar ke zuwa awo. Raliya ke jan motar Na'ima na zaune a gefen mai zaman banza. Raliya ta É—an muskuta ta dubi kawar tata kana ta mai da idanun ta kan titi tare da faÉ—in "Aminiya yanzu yanda kika tsaran nan kina ganin hakan zai yuwu kuwa baza'a sami wata matsala ba dai ko?". Na'ima tasauke numfashi tare da gyara zaman ta cikin karfafawa da gaskata muradin ta tace "Kada ki damu aminiya Nice fa Na'ima baza'a sami wata matsala ba tabbas zai yiwu zai yiwu, yau É—in nan kuwa zan haihu, Raliya ina cikin haÉ—ari dole ne kawai na ai watar da hakan, kinsan kuwa jiya da daddare muna kwance da SALEEM yaÉ—aga rigata yana duban cikin yace shi har yanzu baya ganin garman cikin ciki wata 7 amma har yanzu bai taso ba, kin san me yafi firgitani kuwa?". tayi tambayar tana duban Raliya. Raliya ta girgiza kai cikin takai ci taci gaba da faÉ—in "Aminiya sunan wancan É“atacciyar yarin yar, ya kira min har da min misali da ita, wai lokacin da take da ciki bai cika wata huÉ—u bama amma yaÉ—an taso". ido Raliya ta waro tace "What! ya akayi har ya iya tunota? to gaskiya kawata kada kiyi wasa". Na'ima cikin damuwa da bakin cikin tuno da HAMDAH da SALEEM yayi tace "Shiyasa nake son bin duk wata kofar da zaibi ya tuno da wancan banzar É“atacciyar da ko a muce ko a raye oho, duk wata kofar zanbi na toshe duk da nasan bayida wani kataÉ“us, ko da ya tuno tan ma, amma ni kwata-kwata bana son na rikajin kwatankwacin irin sunan ta a bakin sa, bakiji abun da boka yace min ba, yana son yara sosai hakan zai iya yin tasiri wajen rika tuno ta da ita da abun da ke cikin ta duk da hakan ba wani abun damuwa bane amma ni dai sam bana son jin kalmar sunan ta kan laɓɓan sa, to ko yau da safen nan ma muna kwance dashi yaÉ—aga rigata yana shafa cikin yace wai anya abun da ke cikin nan yana da lafiya kuwa shi baya ganin yana girma, nace masa ai jikina yabi Allah ya taimaka ma ina da tumbi,ke nifa kullum a narka abinci nake aciki na in kika ga abincin da nake ci yanzu wai dun kawai tumbi na ya kara girma, yanzu Raliya cikin nan wata 7 ne yana daf da shiga wata 8 yazama dole na É—au mataki in ba hakaba komai zai iya É“aci, kin ga wancan hatsabibiyar kanwar tasa Rafee'at ranar da muka haÉ—u a gidan su har habai ci take min wai mai cikin tuwo, ni har na fara zargin ko ta gane ne". Raliya ta saki dariya har tana dukan sitiyarin motar tana faÉ—in "Ai wannan Rafee'at É—in shegiyar gaske ce sai ana taka mata burki". dai-dai nan suka isa get É—in asibitin, hon Raliya tayi mai tsoron bakin get É—in yawan gale musu get. a gefe in da aka tanada dan ajiye motoci suka faka suka fito suka nufi cikin sibitin. kofar wani office direct suka nufa tare da yin knocking, daga cikin office É—in aka basu izinin shigo wa. wanda ke cikin office É—in yana zaune cikin shigar likitoci yana ganin su ya washe baki tare da faÉ—in. "A'a manyan kasa kune tafe?". cikin fari da ido Raliya taja kujerar da ke fuskantar sa ta zauna tana faÉ—in. "Kanana dai ai kune manyan kuna zaune AC na ratsa ku kuÉ—i na shiga yadda yakamata me yamuku saura?". Na'ima ma kujerar taja tazauna kana suka shiga gaisawa, suna É—an taÉ“a hira da dariya sakanin su da kagan su kasan tabbas sunyiwa juna farin sani. Dr Mukhtar Lawan abokin su Na'ima ne sosai abota ne na tun a makaranta duk kanin su gar tasan garne, duk wani iskanci da sheke ayar da sukayi lokacin suna makaran ta tare sukeyi, har kuma yanzu wani kullin tare suke tufke shi. acikin su shine kaÉ—ai yaÉ—an maida hankali kan karatu har yake cin moriyar karatun da yanzu yake a matakin Dr, asibitin mallakin sa ne wan da mahaifinsa yagina masa bayan zamowar sa Dr. duk hirar da suke Dr Mukhtar idanunsa a kan Raliya,yakafe kirjin ta da ido wan da É—inkin rigar jikin ta ya bayyanar da nonuwan ta kusan rabi a waje. fiki-fiki yayi da ido cikin yanayin shiga tarkon Raliya yadubi Na'ima kana yace "Na'ima kawarki Raliya takini fa taki na ganta kwata-kwata yanzu ko waya na kirata muÉ—an haÉ—u taki ta bani da ma mu haÉ—u, sabo da tasami manya wan da suka fimu bata hurÉ—a da mu". yakarashe maganar da mai da idanunsa kan Raliya wacce tadaÉ—a bankaro kirji tana wani fari da ido. dariya Na'ima tayi tace "Kai haba aminiya ai ko ba komai dai zakizo wannan haÉ—aÉ—É—en office É—in kiÉ—an rika É—ebe maba kewa." fuska Raliya ta yamutsa cikin salon kwarewa a harkar bariki takuma bankaro kirji yayin da yatsarta guda ke saman wuyan ta tana É—an yawo da shi har zuwa kirjin ta, ta saman nonuwan ta,ido ta kanne a kansa kana tace. "Dr kenan ku abun naku ai sai a hankali in ka shirya yanzu Na'ima ta wuce ta bamu guri amma yanzu zaka ajiye min rabin miliyan anan shima É—in dai-dai azo sallama ne". tanuna saman table É—in gaban sa. ido ya waro da karfi ya furta "500k ai ko ai kina na wata guda bai kai rabin miliyon ba". dariya duka suka saka. Dr Mukhtar yace "Ina kinji ko Na'ima kawar ki tafi karfi na sai dai mugani kawai mu latse baki, ko za'a É—an taimaka min naÉ—an lallasa ne basai ciki ba iya waje kawai". yakarasher maganar da dariya haÉ—e da tsigar zolaya. baki Raliya ta taÉ“e tana faÉ—in "Yanzu dai muyi abun da yakawo mu, Dr muna da damuwa fa". Na'ima ta karÉ“i zancen da faÉ—in "Kwarai kuwa Dr akwai matsala". yace "Wani damuwa kuma ai ni a tunani na yanzu bakuda wata sauran ragowar damuwa ke Na'ima da kike da SALEEM a hannun ki". "A'a Dr gaskiya da saura nasame shi kam amma da saura munaso mukuma samin shi sosai yazamo nawan da gasken gaske". zaman ta ta gyara da kyau ta daÉ—a fuskantar shi kana tace "Dr yau nazo haihuwa". ido yawaro yace "Haihuwa kuma antaÉ“a haihuwar da ba ciki?". yafa da dariya sai kuma yakuma sakin dariyar shakiyyanci yace "To ai cikin naki baikai na haihuwa ba tukun". wani goron numfashi ta sauke kana ta daÉ—a gyara zaman ta da kyau tace "Dr tunani na kenan ranar da cikin nan zaikai na haihuwa, ace ciki yayi wata tara yaya zanyi narasa yanda zanyi, rabon da naji wani abu yasani shiga damuwa irin haka na mance, Dr taya zanyi nasami É—a kune manya aikin kune kunfimu sanin yadda za'ayi". jakar hannunta ta aje gefe kana taÉ—aura hannayenta biyu kan teburin gaban su sannan tacigaba da faÉ—in. "Ko nawa ne zan biya har idan nima bukatata zata biya". ÆŠan shiru yayi yayin da yake É—an juyawa kan kujerar da yake kai, sannan yasauke numfashi kana yace "Gaskiya wannan buka taki babbace a gaskiya yanzu samin É—a a cikin asibitin nan da kamar wuya, yanzu an saka matakan tsaro iri-iri, kinsan kwanaki fa munyi ta shari'a da wasu mutane wan da mukayi musu canjen É—a,munyi ta samin matsala dan ma allah ya rufa asiri, amma mezai hana tun da kince kinason É—an cikin gaggawa kije gidan marayu, gidan marayu yakamata kije, akwai wan da suka haifi Æ´aÆ´a zaki iya samin wan da yau ma ta haifa ta yar aka samu aka kai shi gidan marayun, to inaga kije ki É—auka a can É—in zaifi". kai Raliya ta jinjina alamun gamsuwa da shawarin nasa tace "Eh gaskiya hakan ma kawai za'ayi gidan marayun zamuje mu samo É—an acan kagama babu wanda ya isa ya zarge mu, sukuma hukumar gidan marayun zamusan yadda zamuyi da su tun da akwai Æ´aÆ´an banki". Shiru Na'ima tayi yayin da ta zurma cikin tunani naÉ—an wani lokaci kana ta ce "To shike nan amma kuna ganin baza'a sami wata matsala ba ko?, dan nifa bana so maganar tafita naso ace munyi shi anan sakanin mu basai ansako wasu ciki ba". Dr Mukhtar yace "Ai samun É—a a gidan marayu shine kawai mafita kuma rufin asiri, tun da jakar ku na cike da makullin kulle bakin wasu ai an gama, idan mukace a nan ne zamu samu to za'a iya samin matsala dan har yanzu asibitin nan idon hukuma yana kansa sun saka ido sosai suna jiran suji wani abun yakuma fita su sami mafakar hujjojin da suka tara, wan da naki bada damar hujjar tasu tayi aiki idan da kuÉ—i meye bazamuyi ba". ido Raliya ta kanne tace "Wai wan da kayiwa ai kin nan nawa ne yabaka haka?". wani munafukar dariya yayi kana yace "Miliyan 10 tabani kuma ko wani wata ina É—aukar albashi daga gurin ta". "Bayan 10 million tana kan baka wani kuÉ—in kuma?". Na'ima tayi maganar da fuskar mamaki. yace "To ai kin wasa nayi mata kaÉ—an fa yarage yataÉ“a nawa aikin dan ma Dad yatsaya da gaske kan lamarin, canjin É—a ai bakaramin kasada bane, jigo na canza mata da shi É—a na miji na musan ya mata da mace, to kuÉ—in wasa suke samu a kasar nan 10 million wani kuÉ—i ne agurin su, duk wata 300k nake É—au ka a gurin ta tukuicin godiya." dariya suka sheke da shi cikin muryar dariya Na'ima tace "Kai Mukhtar wlh bakada dama shine ko É—an salalan nan babu." "Haba wani salala ke me zakiyi da kuÉ—i yanzu kinada jakar kuÉ—i a gefen ki, kinada ABDALLAH IDRIS ABDALLAH me kuma zakiyi da kuÉ—i, ai nine abun a taimaka dan ko Raliya kuÉ—in da take samu bani samun irin sa". mikewa Na'ima tayi tana faÉ—in "Kace dai bazaka bamu ba kawai musan in da muka ajiye ka, aminiya tashi mutafi gidan marayun nan yanzu ba'a bori da sanyin jiki". zai yi magana sai kuma yayi shiru sakamakon hayaniyar da yaji ke É—an tashi daga can waje da alama a cikin parlou'n asibitin ne in da mutane ke zama dan jiran ganin likita. wata nurse ce ta shigo bayan tayi knocking an bata izinin shigowa, É—an rusunawa tayi tace "Sir gawasu sun zo da alama haihuwa ce sai dai basuzo da kayan haihuwa ba, nace sukawo kuÉ—in kayan haihuwar sunce basuda kuÉ—i,nace to su koma suzo da kuÉ—i sunki tafiya, kuma yara ne dukan su nayi ta tuhumar su ina iyayen su sunyi shiru na ce suje su kira babba san nan su taho da kayan karÉ“ar haihuwa ko kuÉ—in kayan tunda akwai anan sunki tafiya,kuma da alamu labour take sosai zata iya haihuwa cikin mintuna kalilan gasu can zaune a parlour sunki tafiya." Dr yace "Yara kuma? akira su su shigo." tace "Okay sir." tajuya da sauri ta fita, jim kaÉ—an suka shigo, tana gaba Æ´ammata biyu na biye da ita É—aya da ciki rukuku É—ayar kuma tana tallafe da ita, sanye da uniform ajikin ta. da kaga mai cikin da alama nakuda take sosai dan sai tauna baki da yarfe hannu take tana ta faman zubda kwalla da faÉ—in "Wayyo nashiga uku." Dr yadubi wacce suke tare da mai cikin yace "Me yake faruwa wace matsalar ke tafe da ku?." tace "Haihuwa tazo shine na rako ta." Na'ima da Raliya kuwa ido suka zubawa yaran wan da akalla shekarun su bazai wuce 16 ba. Dr Mukhtar yace "Ke kaÉ—ai kika rakota haihuwar ina iyayen ku?". shiru yarinyar tayi tana duban mai cikin da sai daÉ—a shiga yanayin nakuda gadan-gadan take. sai kuma ta dubi likitan cikin rauni tace "Iyayen ta suna gida nima kawai tazone tace narako ta asibiti." É—an shiru Dr mukhtar yayi idanunsa a kansu kana yace "To ina mijin ki?." yayi maganar idanunsa akan mai cikin. duk kanin su shiru sukayi sai raba ido suke, ido ya kure su da kyau yakuma faÉ—in "Nace ina mijin ta? ita kaÉ—ai zata taho haihuwa babu wani babba ko shi mijin baisan haihuwar yataso bane kirashi a waya yanzu yazo dan bana karÉ“ar haihuwa sai an ajiye kuÉ—i an kuma sa hannu tukun". Cikin kame kame Æ´arrakiyar tashiga faÉ—in "Um..um mijin..ta..mijin ta." sai kuma tayi shiru. duban mai labour É—in yayi da kyau yace "Kirawo mijin ki yanzu yazo kice masa bazamu karÉ“e kiba har sai yazo." kasa tayi da kanta batare da tace komai ba sai hawayen da ke cigaba da sauka a idon ta, girgiza kai yayi kana yace "Ba miji kenan wannan ciki ba uba baya da uba ko?". da sauri Æ´ar rakiyar ta gyaÉ—a kai tana tsilli-tsilli da ido kamar an tare É“era kana cikin in-ina tace "Wlhy likita tsautsayi aka samu bata da miji, kuma yanzu iyayen ta sun kore ta da sukaga tana labour sun ce tafita musu a gida taje can ta haihu ba a gidan suba, shine tazo gidan mu nikuma naga kamar zata mutu shine na rakota asibiti, dan Allah likita ka taimaka mata." gaba É—aya suka zuba musu ido. wani murmushi Raliya ta sake. ido Na'ima ta bita da shi dan tasan ma'nar murmushin nan nata tace "Aminiya sabon shiga harka ko?". baki Raliya ta taÉ“e tare da faÉ—in "Oh yaro man kaza har yaushe zakayi sake irin haka ta kasance, ka É—aukar wa kanka wahala shi ba mai uba ba wahalarka a banza, uban titi da bazai kalleka cikin halin labour yace ma sannu ba, tuni ban wanke shi na zubar ba in ma yasami shiga kenan mttss". taja wani dogon tsaki tare da faÉ—in "Kara mar Æ´ar iska bata san yan da zatayi iskancin bama." Dr Mukhtar da Na'ima kasan cewar suna kusa ne suna juyo duk abun da take fata akasin su da suke tsaye a sakiyar office É—in. Dr Mukhtar yayi murmushi tare da faÉ—in "Ko zaki sata a hanya ne idan ta sauke kayan dake jikin ta". harara ta dalla masa tare da kuma jan wani gajeren tsaki. Dr Mukhtar ya mai da duban sa kan yaran sannan yace "To a gaskiya bazamu karÉ“i haihuwar ba, na É—aya babu kuÉ—in karÉ“ar haihuwa sannan babu wani babba a tare da ku, bazamu karmi haihuwar ba saboda gudun matsala, bugu da kari kuma É—an bashi da uba, muzo mu karÉ“i haihuwa wani abu ya faru azo a dakatar min da asibiti gaskiya yanzu na daina irin wannan kasadar gaskiya kuje kawai kuje wani asibitin." Da sauri Na'ima da Raliya suka juyo a tare tare da yiwa junan su kallon-kallo, sai kuma da sauri Na'ima ta juyo gun Dr tace "Dr a taima musu a karÉ“i haihuwar ni zan biya kuÉ—in duk wani É—awai niyar da za'ayi ni zan biya, zan kuma tsaya wajen ganin ba'a sami wata matsala ba, aje a kaita labour room." kai Dr Mukhtar ya jinjina kana yace "Okay." yadubi nurse É—in yace "Akai ta labour room. tace "Okay sir." tajuya da sauri tana faÉ—in "Kubiyo ni." suka fita dukan su mai labour'n da kawar tata. suna fita da sauri Raliya ta dubi Na'ima zatayi magana Na'ima tayi saurin soma yiwa Dr mukhtar magana. "Dr irin su ne idan suka haihu suke kashe É—an, har idan akabar ta ta tafi bazataje wani asibitin ba wani gun zataje ta haihu ta kashe É—an, ko kuma ta jefar da shi to ni ina son abun da zata hai fa har idan na miji ne." Dr mukhtar yayi wani dariya tare da faÉ—in "Ai tun É—azu na fahimci hakan ai tun da naga kuna wannan kallon-kallon Na'ima Raliya bakuda kyau sai an haÉ—a da wanka, ai na san hali tun a makaranta har idan kukayi wannan kallon-kallon to wata tsiyar za'a kulla." dariya suka sheke da shi suka tafa kana shima ya miko hannu suka tafa da shi dukan su. zaman sa zagyar da kyau sannan yace "To meye kaso na a ciki?." Na'ima tace "Kana da kaso mai tsoka yanzu dai kaje ka bata kulawa ta haihu kuma kayi fatan namiji zata haifa, yau nima zan haihu." yace "kwarai kuwa har an shiga dake labour room". dariya suka saka dukan su. Nan sukayi ta wasu magan ganun su sakanin su batare da ni naji ko fahimtar me suke nufi ba.. Bayan awa uku, kukan jariri ne ya soma tashi daga cikin labour room, Na'ima da Raliya da har yanzu suna zaune a office É—in Dr Mukhtar suka wani saki murmushi, lokacin da sakon Dr Mukhtar yashigo wayar Raliya wato tex message yana sanar musu da abun da aka haifa, ciki murmushin mai kunshe da ma'anoni da dama Raliya tace "Kai sannu Na'ima kin sauka lafiya kai gaskiya haihuwa akwai wuya kinsha fama yau." itama wani dariya ta sake cikin kware wa a zunzurutun makirci da hatsabiban ci tace "Na haihu yau ni Na'ima gaskiya haihuwa a kwai wuya". darika suka kuma shekewa sukatafa. Dr Mukhtar da yanzu shigowar sa office É—in bayan ya amshi haihuwar, zama yayi kan kujerar sa yana faÉ—in "Gaskiya yau ba sauki oga SALEEM ya haihu um wayaga oga SALEEM da É—a abun ba sauki hhhhh". "Shima yazama baba ni kuma mama". Na'ima ta faÉ—a tana wani faÉ—i. nurse ce tayi knocking tashigo taÉ—an dukar da kai tana faÉ—in "Sir an gama kimsa komai sai dai har yanzu tana bledin, munyi iya kokarin mu bai tsaya ba ko zaka zo ka duba ta." kai ya girgiza kana nurse É—in ta fita da sauri, a tare Na'ima da Raliya suka mike ganin Dr shima ya mike sukabi bayan sa. dukan su suka shiga É—akin da aka tanada domin haihuwa. nan da nan yasoma baiwa yarin yar taimakon gaggawa ganin yan da jini ke fita a jikin ta, batare da É“ata lokaci ba tadawo cikin hayyacin ta ,jinin kuma ya tsaya. jaririn da nurse's suka gyara shi suka kunshi cikin É—ankwalin mahaifiyar sa sai musu-musu da kuka yake ga dukkan alama niman abinci yake, nurse ta É—ago shi ta maso gaban gadon da mamarsa take, wan da a Æ´an min tunan da ta sami kanta bayan Dr yabata taimakon da ya kamata har ta iya mikewa tazaune. tamika mata shi tana faÉ—in "Ga abun da kika haifa nan kuma da alama niman abinci yake gashi bakuzo da flas ba, bare a bashi ruwan zafi ya sha." kin karbar sa tayi sai kukan da ta fashe da shi. kawar ta da suka zo tare ita ta karÉ“i É—an tashiga jijjiga shi, wayar ta dake cikin aljuhun wandon makarantar jikin ta yasoma kara alamar shigowar kira,da sauri takai hannunta guda ta cusa cikin aljuhun wan donta, É—aya hannun kuma ta gyara rukon jaririn da kyau ta zaro wayar. ido ta waro kan screen É—in wayar murya cike da tsoro tace "Mama." sai kuma da sauri taÉ—aga kiran takai wayar kunnen ta tare da yin sallama. É—an shiru tayi sai kuma tace "Mama gani nan dawowa an tashi ne bansami abun hawa ba shine yasa na tsaya". tana sauke wayar da sauri tadubi kawar tata tace "Mama ce takira ni taga lokacin tashi yayi har yanzu ban koma gidaba, bayan ko makarantar ma banje ba,ni sai yanzu ma na ga agogo tun É—azu lokacin tashi yayi, tofa zantafi gida yanzu yaya zamuyi ina tsoro kada Baba yadawo yasamu ban dawo ba, kema zaki tafi gida ba kawai tun da yanzu kin haihu? muje na rakaki gidan ku nima sai na wuce gida, karfa Mama tasa yayu na su biyo ni kin san fa in nakai wannan lokacin sawa take aje a nimo ni". tana maganar ne cikin tsaro sosai. itako mai jego kuka kawai take takasa cewa komai. Dr yace "A'a taya za'ayi ta tafi yanzu bayan yanzu ta dawo hayyacin ta,sai mun daÉ—a ganin yanayin jikin nata kafin mu sallame ta, yanzu kam ma allurar da akai mata zai fara ai ki in tayi bacci ta farka mukaga yanayin karfin jikin ta sai mu sallame ta, yanzu dai ke kije tun da ke a na kiran ki." to tace da sauri ta mika mata É—an, yanzu ma kin karÉ“ar É—an tayi. Raliya ce ta karÉ“i É—an a hannunta tace "To kije kawai." ai ko tafita da sauri. bayan fitar ta Dr Mukhtar ya dubi yarinyar yace ta kwanta ta sami bacci, a hankali ta gyara kwanciyar ta,su kuma suka fita suka koma, office É—in sa. suna zama Na'ima tace "Bani É—an na ganshi." Raliya ta mika mata kyakkyawa fari kuwa da shi, sai dai yaron bashida girma É—an kankani ne hakan kuwa bazai rasa nasaba da rashin samun kulawa da ya kamata tun aciki ba. takafe shi da ido tana wani irin murmushi tana É—an jijjiga yaron. after 4 hr. hakan kuwa yayi dai-dai da farkawar yarinyar da ta haihun a bacci, alhmdllh taji karfin jikin ta kwarai. nan tanimi tafiya gida nurse tazo ta sanar wa Dr yace taje ta kira ta. tare nurse É—in suka shigo da yarin yar,ya nuna mata kujera ta zauna kana yacewa nurse É—in taÉ—an basu guri, nan ta fita tajawo musu kofa. duban yarinyar yayi kana ya ce "Inane gidan ku". cikin kame-kame tashiga faÉ—in "Um..um..gidan mu gidan mu." sai kuma tayi shiru. da kyau yakuma duban ta sannan ya ce "Bana son wani É“oye-É“oye nasan wannan É—an bashi da uba cikin shege ne dan haka kawai tan bayar ki nake ki bani amsa inane gidan ku?." kwalla ta matse tare da mutsutstsike yatsun ta kana ta soma magana, "Gidan mu yana..yana Unguwar Bakaro". kai ya jinjina yace "A Bakaro kike?." ta gyaÉ—a kai, Raliya ta jinjina kai kana ta ce "Ah to shikuma uban É—an a ina yake shima a Bakaron yake?". tace Eh. "To yan zun ina zakije keda É—an idan kika fita daga nan?". Raliya tayi mata tambayar tana dubam ta, shiru tayi tare da musutssuke yatsun hannunta. Dr Mukhtar yaÉ—an tsura mata ido kana yace "Yanzu ina zaki kai É—an idan aka baki shi?." kuka tafashe da shi tana faÉ—in "Wlh idan na tafi da shi gida yan kani za'ayi wlh iyayena sun ce sai sun yanka ni yanzu ma in na koma gida nasan suka na za'ayi idan na tafi da shi zasu yanka ni". kuka take sosai tana faÉ—in zasu yanka ta, Na'ima kuwa carap tayi tace "To ni zan rike miki É—an ni ina son shi nasan idan kika fita yaddashi zakiyi ko ba haka ba?". tafaÉ—a tana duban ta. da sauri yarin yar ta gyaÉ—a kai tace "Wlh in natafi da shi gida ne za'a yanka ni in naje dashi gida ne." Na'ima ta ce "To ya isa, in kika je da shi gida ne za'a yanka ki idan kika fita da shi daga nan kuma yaddashi zakiyi to ni ina son shi zan rike shi". hannu ta saka ta buÉ—e jaka ta ciro kuÉ—i masu yawa gudan dubu-duba ne a É—aÉ—É—aure É—auri uku,wacce a kalla ko wani É—auri guda yakai 100k ta mika wa yarin yar tana faÉ—in "KarÉ“a in kinje kya nima abun da zaki rika ci wan da yakamata masu jego suci, ba sai kin jira iyayen ki sun yi miki ba tun da nasan cewa bayimiki zasuyi ba, da ma ace É—an da uba ne tun da bashi da shi kuwa ba mai saurarar ki, gashi sai kije kiyi jego shikuma É—an ina son shi zan rike shi, dan bazan iya zuba ido ina gani azalinci É—an da baiji ba baigani ba ku mutane kurika jin tsoron Allah, É—an da bai san komai ba aje a jefar da shi ko a kashe shi." da sauri yarin yar ta mika hannu ta karÉ“i kuÉ—in har hanunta na rawa ganin yawan kuÉ—in, kana ta yimusu godiya ta mike da sauri ta fita, har takai bakin kofa Na'ima tace "Idan kikaje gida aka tanbaye ki ina abun da kika haifa sai kice yana ina?." "Ya mutu tun a ciki!." tayi maganar cike da karfafawa tana daÉ—a dunkule makudan kuÉ—in da ta bata. murmushi Na'ima tayi tare da faÉ—in "Da kyau." da sauri yarin yar tayi waje ta haye abun hawa ta wuce gidan su cikin zillumi da tsoro.. bayan fitar yarinyar Raliya da Dr Mukhtar suka tuntsire da dariya, cikin muryar dariya Dr Mukhtar yace "Kin ji Na'ima har da É—an guntun wa'azin ta wai ku mutane kurika jin tsoron Allah tun da kin samu a sama ai dole kijefo wa'azi ciki hhhhh." "In da kuÉ—i meye bazan samu ba kai bakaji takashe É—an nata tun a ciki ba, wannan kuma ni na haifa." tayi maganar tana leko fuskar yaron da yake baccin sa. Dr mukhtar ya gyara zama tare da sauke numfashi sannan ya ce "To yan zu ya za'ayi ne?." tace "Dr ni da na haihu kuma me yazaunar da ni a nan a kaini labour room mana." dariya ya sheke dashi Raliya ma dariyar tayi tana faÉ—in "Ai kuwa mai jego a gado yakamata a same ta a kwance ba'a zaune a office É—in likita ba." nan suka mike suka nufi labour room bayan sun gama shirya duk yan da abun zai tafi. suna shiga ta haura gado ta kwanta, tayi shame-shame kamar wacce ta haihu da gaske. Waya Na'ima ta mikawa Raliya tace "Kirashi a waya". Raliya ta amsa ta danna number SALEEM......! Mommyn Twins ce 8/19/22, 10:50 - Ummi Tandama😇: 🌺 *HAMDAH* 🌺 *WASA FARIN GIRKI!!*âœðŸ? *NA* *RASHEEDA S DIRECTOR* _(Book 3)_ Littafin na siyar wa ne ki biya ki karan ta. domin biyan kuÉ—in littafin sai ka-ki tuntuÉ“i wannan number 08034690723 🅿ï¸?2 Wayar tayi ta ringing har ya yanke bai É—aga ba, ta dubi Na'ima tace "Bai É—aga bafa. " ta ce "Sake kiran shi kin san shi ai murÉ—aÉ—É—en mutum ne idan baiyi ra'ayi ba bazai É—aga ba yanzu haka wayar tana kusa da shi É—agawar ne dai baiga dama ba." kuma kiran nasa tayi namma har ya yanke bai É—aga ba, sai da ta kirashi har sau uku a na huÉ—u ne ya É—aga. ganin ya É—aga kiran takai wayar kunnen ta tare da faÉ—in "Asslamu'alaikum SALEEMA Raliya ce muna asibiti da Na'ima tahaihu." SALEEM dake zaune a office yana ta tarkasa Æ´an kayakin sa dan locin tashin sa yayi har ya wuce ma, Æ´an wasu aiyuka ne suka tsaida shi. yamike zumbur yana faÉ—in. "Haihuwa kuma? yaushe cikin nata yakai na haihuwa cikin ya fita kenan?." yajero tanbayar da alamun hankalin sa a É—an tashe yake. ta ce "Eh haihuwa ce ba fita cikin yayi ba sai dai bakwaini ta haifa É—a na miji." numfashi yasauke jin akasin abun da yake zato,shi gaba É—aya jin lamarin na bazata ya mantar da shi zata iya haifar cikin tun da yakai wata bakwai, ya ce "Ina jaririn yake yanzu yana cikin wani hali yana dai lafiya ko?." "Eh gashi can a cikin kwalba." katse wayar yayi batare da yace komai ba, Na'ima da take jin duk abun da yake faÉ—a kasan cewar tasa wayar a amsa kuwa ne ta ce "Lallai ma wannan wato shi ta jaririn yake bazai fa taÉ“a sauyawa duka ba." dariya Raliya tayi tare da faÉ—in "SALEEMA kenan miskili kafi mahaukaci ban haushi bafa zai sauya ba dan kuwa a jinin sa yake." SALEEM na kashe wayar, wayar Mamie ya kira, zaune Mamie take da su Aunty Rafee'at Aunty Jaleela da su Ummi kiran sa ya shigo. bayan sun gaisa yake faÉ—a mata Na'ima ta haihu. "Haihuwa." Mamie tafada da karfi kana ta ce "Wani irin haihuwa ciki wata bakwai." ya fuskanci yanayin da yashi ga lokacin da Raliya ta sanar masa da haihuwar shi Mamie ta shiga yanzu. yace "Eh ta haihu bakwaini ta haifa tana asibiti ma yanzu." "To Allah ya raya." Mamie ta faÉ—a a takaice tare da kashe wayarta. gaba daya hankalin Æ´an cikin parlour'n yakoma kan Mamie, Ummi ce da sauri tace "Wa ta haihu Na'ima ce?". Mamie tace "Wai haka, wai ta haihu". Mamie ta faÉ—a tana taÉ“e baki. Ummi ko baki ta washe tana fadin "Ikon Allah, kaji ikon Allah ko to Allah dai yasa abun da aka haifa nacikin koshin lafiya". baki Mamie takuma taÉ“ewa tare da faÉ—in "Ina kuwa zai zama cikin koshin lafiya ciki wata bakwai sai dai yabada wahala dai". a É“angaren Aunty Jaleela ma fuska ta yamutsa tana faÉ—in "Gayyan wahala dai ciki wata bakwai ai ba arziki." "Ina kuwa arziki duk uban iyayi da cikin ashe dai rabin halitta za'a haifo ba arziki." Aunty Rafee'at ta faÉ—a, tana tura É—ankwali gaban goshi. duk kanin su in ka gansu babu wani mai farin ciki da jin daÉ—in haihuwar, akasin Ummi da fuskarta ke É—auke da annuri bakin ta ya kasa rufuwa sai faÉ—i take "Kai masha Allah Allah dai ya raya mana." mikewa Ummi tayi tana cigaba da faÉ—in "Kai masha Allah zamu wuce asibitin ba yakamata mu tafi asibitin yanzu". Mamie ta kawar da kai gefe tare da faÉ—in "Ummi'n Fauzan ni gaskiya ba yanzu zanje asibitin nan ba gaskiya inaga kamar ina da abun yi, ai dare yayi yanzu ga magriba yakawo kai." Ummi ta girgiza kai tana faÉ—in "Kai Mamie'n Nusaiba yakama ta dai muje yanzu ace babu wani nashi a can gaskiya baiyi ba." fuska Aunty Rafee'at takuma yamutsawa tana faÉ—in "Um ni kamma kucire ni a tafiyar dan yanzu Abba'n Adeel zaizo ya É—auke mu." dakuwa Ummi tayi mata tare da faÉ—in "Maza tashi kushirya ke Jaleela tashi maza muje". Aunty Jaleela da tazo har wuya ta kwaÉ“e fuska kana tace "Ni wlh ina ji ma kamar kar inje dan nima Daddy'n Fadeel nasan zai zo yanzu." haÉ“a Ummi ta rike tana sallallami da kyar dai ta tirsasa musu ta samu suka fita, suka nufi asibitin bayan sun sanar wa su Abbu. A asibitin suka tadda SALEEM shima isowarsa kenan a tare suka shiga cikin asibitin. direct É—akin hutu suka nufa in da nurse tayi musu jagora zuwa ciki,take sanar musu da cewa an mai da Na'ima can domin ta huta. nan suka tadda Na'ima kwance tana ta sauke numfarfashi Raliya na tsaye a kanta tana ta yi mata sannu. da sauri Ummi ta matso in da take tana faÉ—in "Sannu sannu kinji Na'ima, kin sami kanki kalau?". dakyar ta buÉ—e baki cikin yanayin mutum yasha wuya murya can kasan makoshi tace "Lafiya lau." Mamie ko kallo É—aya tayi mata kana tace mata Sannu. namma da kai ta amsa. Aunty Rafee'at kam ko kallo bata ishe taba, Aunty Jaleela ce ma a sama tace mata sannu ita ma. Ya SALEEM da ya naÉ—e hannu a baya yana tsaye tagurin kafafun ta yadan dubeta kana yace "Ina yaron yake?". Raliya tace "Yana can ansashi a kwalba. kai ya jinjina cikin yanayin nan nasa, ya maida duban sa kan nurse É—in da ta yimisu jagora yace "Muje a nuna mana in da yake, ina Dr yake?". ta ce "Yana office". fita sukayi duka har da Raliya, Raliya tayi saurin shigan office É—in Dr tare suka fito da shi, ya mikawa Ya SALEEM hannu suka gaisa ba yabo ba fallasa Ya SALEEM ya amsa masa gaisuwar, kana ya gaida su Mamie sannan ya wuce dasu É—akin da aka ajiye jaririn wan da yake karkashin kulawar na'urori.. Can suka hango jaririn cikin kwalba wan da ake saka jariran dabasu kai watannin haihuwa ba, yanata wutsul-wutsul da kafafunsa. murmushi Raliya tayi a kasan ranta dan ganin shirin su yana tafiya yan da ya kamata. da sauri Ya SALEEM ya karasa jikin kwalbar yana leka cikin kwalbar. su Ummi ma gaba É—ayan su suka karaso jikin kwalbar, Ido Mamie ta kurawa jarijin da ake kiran sa da bakwaini gashi dai ba wani girma yake da shi ba É—an kankani ne, sai dai yanayin sa da wayon faskarsa ya girmi na bakwaini. kai ta girgiza tare da juyawa ta kalli likitar tace "Wannan shine bakwaini an ya ma kuwa anyi lissafin cikin nan dai dai ko dai tara ne an É“ata lissafin kaga yaron da wayon sa." da sauri Raliya tace "Bai cika tara ba bakwai ne ai ko jiya ma sai da mukayi lissafin watannin da ita, yau kuma sai ga haihuwa kingan shi ai É—an misilili da shi". Ummi tace "Ai kuwa gashi É—an kankani irin su idan suka tashi girma sai an gansu dan sai anci tuwo an koshi kafin a iya É—aukar su". Ya SALEEM kam duk baya jin su dan ya gama shagalta da kallon yaron wai shine yau da É—a, wannan É—an nasa ne, wani murmushi yayi a kasan ransa wan da har sai da yabayyano kan fuskarsa. Aunty Rafee'at data kafe yaron da ido tarr sai lokacin tayi magana. "Wai wannan yaron shine bakwaini gaskiya wannan baiyi kamada bakwaini ba sai dai in ku kuka É“ata da lissafin". tayi maganar cikin gatsali. wani kallon sama da kasa Raliya ta bita da shi. Aunty Rafee'at ma irin kallon ta wasa mata tare da girgiza kai tana cigaba da yi mata wani kallon shekeke, sannan ta juya ta fita a cikin É—akin bayan ta gama ai kawa Raliya kallo masu cike da ma'anoni da yawa.. ko minti 30 basuyi a asibitin ba Mamie tace sutafi, haka dai suka fita suka koma gida. Haushi da bakin ciki kamar Na'ima tayi yaya, wai ace kalar gaisuwar da surukar ta zata yi mata kenan, babu wani gaisuwa mai nuna tausaya wa babu wani nuna farin cikin samo mata jika da tayi. Raliya tace "Ni da É—ina da ke gajen hakuri dan Allah kibar wannan maganar kiyi shiru, ke kam dai ba kin haihu ba ina ruwan ki da su, wan da kika haifa masa ne idan ya miki zakiji zafi,ina ruwan ki da su ba wa É—an su kika haifa ba, can ta matse musu ke meye damuwar ki, kinga wannan shegiyar yarinyar zan nuna mata ni Æ´ar bariki ce cikakkiya ma kuwa ciki da waje na, wai shegiyar Rafee'at É—innan kinga wani kallon da take min, kinga wani kallon da take min kuwa, zan nuna mata halina bata sanni bane." Na'ima tace "Him in dai wannan Rafee'at É—in ce ta wuce sammanin ki, wannan yarin yar da kike gani nima inada cikin ta kuma zanyi maganin ta, zan je musamman gurin boka domin yamin maganin ta, zatagane da ni take rabu da ita mance da ita dan wlh sai ta gane kuskuren ta." Jin an murÉ—a handle yasasu yin shiru da zancen nasu, Na'ima ta gyara kwanciyar ta kamar É—azu, ta daÉ—a marairace fuska da shagwaÉ“e fuska. ya karaso bakin gadon yadube ta kana yace "Ya jikin?". cikin makirci da salon iya kirsa tace "My SALEEM kaga É—an mu ko,ya bani wahala yaron nan, É—an ka yabani wahala My SALEEM da kyar na iya haifo shi." gefen fuskarsa ya shafo tare da naÉ—e hannun sa É—aya a bayan sa, "ÆŠa na." yafaÉ—a a kasan zuciyar sa yayin da yake jin wani abu yana tsarga masa mai kama da farin ciki, can karkashin kasan zuciyar sa kuwa, jin wani abu mai nauyi yake yana kokarin tasowa sai kuma yanayi biyun suka shiga kokawa da junan su, yayin da farin cikin ya danne wancan nauyin da yake jin nauyin sa na yau yafi na kullum. har sai da yakai hannu ya dafe kahon zuciyar sa. daga Na'ima har Raliya ido suka zuba masa ganin yan da ya dafe kirjin sa da karfi tare da rumtse idanunsa, wani abu ne ya gilma masa cikin duhuwar kwayar idanunsa da suke a rufe, wani irin bugawa kirjin sa yayi kamar an fizgi zuciyar sa, sai yarika ganin wasu abubuwa guda uku masu haske suna yi masa yawo cikin ido yayin da bugun zuciyarsa ya tsanan ta, dai-dai lokacin da yaga abun suna daÉ—a tunkaro sa tamkar suna tahowa gare sa, a zahiri kuma idanunsa a buÉ—e. sai kuma a sannu suka rika yin nesa dashi sai da sukayi nesa dashi sosai kana duhu takuma gilmawa sakanin su. cikin tsananin karfi ya ware idanun sa, jin muryar Na'ima tana faÉ—in "Ya dai My SALEEM?". hannayen sa biyu ya cusa cikin sumar kansa kana ya burzar da wani huci mai zafi daga bakin sa "I'm sorry." ya faÉ—a tare da juyawa yabar É—akin da sauri, yayin da yake jin zuciyar sa naciga da yi masa nauyi, acikin Æ´an kwanakin nan hakan yana yawan faruwa da shi akai-akai, musamman in ya kwanta bacci yarika irin wannan mafarkan kenan, sai yari ganin haske guda uku suna dumfaro shi sai sunzo daf da shi sai su bashi baya yayin da duhu kuma zatazo ta mamaye hasken. abun da yake gani cikin mafarkin sa shi ke kokarin zuwa masa a zahiri, to ko bacci yafara a tsayen har ya fara mafarkin?. yarika jefowa kansa tambayoyin da bashida amsar su.. Bayan sa Na'ima tabi da kallo cikin takai ci, a tunanin ta É“arin jiki zaiyi idan yaji ta haihu, idan yaga É—an kuma murna zai yi ba adadi, sai kuma gashi sai wani shashshan kamshi yake,batare da ya nuna farin ciki da hakan ba. A can kuwa bayan komawar su Mamie suna tare a parlour kowa na faÉ—an albarkacin bakin sa. Mamie kam sam taji wannan É—a bai kwanta mata a rai ba, kwata-kwata taji É—an baya cikin ranta, tana yi masa wani irin kallon da ita kaÉ—ai tasan ma'anar sa. Aunty Rafee'at fuska ta yamusa ganin su Fauzan da Nusaiba na ta murna wai matar Ya SALEEM ta haihu zasu sha suna tace "Dalla kurufa mana baki, ni wallahi wannan É—an ma kwata-kwata bai min ba wlh ya É—auko jinin uwar sa, ni bai min kama da bakwai niba haka bakwaini yake,sau nawa nake ganin Æ´aÆ´an da ake haifarsu wata bakwai sai ace wai wannan É—an wata bakwai ne, to can ta matse mata sai taje ta ta fama taje can tayi ta haifar bakwaini ita ta sani". kai Mamie ta girgiza. Aunty Jaleela tace "Ai wlh nima Aunty Rafee'at É—an baimin kama da É—an bakwai ba, sai dai idan ko sun É“ata lissafi ko kuma wani munafurcin ta ke kullawa ciki yafi wata bakwai tace bakwai to meye amfanin hakan, meye na cewa ciki wata bakwai bayan tasan cikin yafi bakwai É—in". Ummi ko cemusu tayi "To ku in ban da abun ku ta yiwu ta É“ata da lissafin ne in mutum ya É“ata da lissafi kam shi zai rika lissafi kuma alhalin ba haka bane, ai ba wani abu bane kakan iya É“ata da lissafi, kuma ai ana iya haifar wata bakwai yayi rai me lafiya ma yatashi har yafi É—an wata taran kwari da kuzari, kar ku mance fa a asibiti ta haihu in ba bakwai ba taya za'ayi a sashi a kwalba likitan ai yafiku sanin me yake, Allah dai ya rayashi da imani". "To amin". cewar su dakaji amin É—in kasan baikai can kasar zuci ba... Bayan kwana uku tun da sukaje sau É—aya basu kara zuwa ba sai ranar da ta cika kwana uku shima da kyar Ummi tasa Mamie suka koma asibitin, anan suka tadda Æ´an gidan su Na'ima, nan ma basu wani jima ba suka baro asibitin. satin su Na'ima biyu a asibitin, zaune suke da kawar ta Raliya Na'ima ta dubeta tana faÉ—in "Kai Raliya wlh nagaji da zaman asibitin nan haka, wai shin dole ne sai mun yi wata biyu a asibitin nan, dole wai saimunyi wata biyu wlh nagaji da zaman asibitin nan, wai dole ne har sai É—an yacika wata tara kafin mu koma gida, gaskiya asan yan da za'ayi kije ki sami Dr asan yan da za'ayi gaskiya, wlh nagaji da zaman asibitin sati fiyu fa ina nan,gaskiya kije ki same shi asan yan da za'ayi nakoma gida." Raliya tace "Gaskiya nimafa nagaji da sintirin yau asibiti gobe asibitin nan,kullum kenan mutum na hanyar zuwa asibiti alhalin duk kanin ku lafiyar ku lau, jariri yana nan yana shan madarar sa ke kina nan kina narkar abincin ki, nikam mafa inada wasu a hannu wlh ina da wan da na karÉ“i kuÉ—in su, akwai wan da na karÉ“i kuÉ—in sa na kwana uku gashi nan ko wuni É—aya bamuyi da shi ba, sakanina da shi da daddare mu kwana shi da yaso muje Abuja muÉ—an shana, gaskiya bari naje na samu Mukhtar asan yanda za'ayi ki koma gida, nasamu naje su fanshi kuÉ—in su". ta karashe maganar tana mikewa tsaye ta fita ta nufu office É—in Dr. Bayan Raliya sun gama tattaunawa da Dr Mukhtar yace "To gaskiya akwai yadda za'ayi zata iya komawa gida abisa ita ta tirsasa tagaji da zaman Asibitin, nikuma sai na bada wasu shawarwarin da zata É—auru akai bayan ta koma gidan". nan suka tsara yan da abun zai tafi. a ranar da yamma suka sami sallama suka koma gida, bayan shariÉ—oÉ—i da shawarwarin da Dr ya bata a gaban Æ´an uwan ta da kuma gogan wato SALEEM. Tun da suka koma gida yaron kullum a kwance yake idan akazo barka ma sai tace ba'a É—au kar sa sabo da likita yace, kada a rika yawan sa masa hannu, sai dai azo a ganshi a kwancen kawai acikin bargon da kullum yake dukunkune a ciki. haka tayi ta rainon É—an da masu da ita da É—an ma'aikatan ta da kuma Æ´an uwan ta, koda waÉ—an da suke kanta sukaga nonon ta ba ruwa basu kawo komai ba sai cewa sukayi ai dama gaka wasu matan suke sai an nimi magani. tuni aka nemo maganin wanke nono da ku ma ruwan nono, kan kace me ruwan nono yakawo tashiga shayar da É—a. lokacin da suka cika wata biyu,wato É—an yacika wata tara kenan washegari tahaÉ—a wani gagarumin taro. biki irin na masu ji da naira, biki akayi na gani na faÉ—a naira tayi kuka, ranar SALEEM katuwar saniya ya yanka da katon rago, yaron yaci sunan baban Na'ima. ko da taji sunan da ya raÉ—a masa sam bata so ba dan taso yayi wa babansa ne takwara. yace mata shi halacci yayi mata yasa wa É—an sunan mahaifin ta. ranar kuwa kaÉ—an ya rage Raliya suyi faÉ—a da Aunty Rafee'at kan cewa da Aunty Rafee'at tayi yaron ma ko kama da su baiyi ba duk da kuwa girman da yake ta karawa,amma ko alamar kama da su bayayi sai dai in ya É—auko zuriyar uwar sa dan ko kama da uwar tasa ma baiyi ba. shike nan kawai suka kama zasuyi faÉ—a, wai akan me yasa Aunty Rafee'at zatace haka ai duk wan da yaga É—an yaga SALEEM, dan kuwa farin SALEEM É—in ma ya É—auko tun da kuwa yayi kama da uban sa ai ba sai yayi kama da dangin uban sa ba. cikin masifa da bala'i da tsagwaran bariki Raliya take maganar. Aunty Rafee'at ma kuwa bata yi mata da sauki ba tayi mata wankin babban bargo. Allah ma ya taimaka Ummi tazo sunan ita ta raba faÉ—ar. ta kora Aunty Rafee'at da Aunty Jaleela tace duk su tafi an yafe musu sunan, dan ganin abun na daÉ—a girma dan har Aunty Jaleela tashiga faÉ—ar.... After 1 year Acan kasar Saudi Da sauri na fito daga cikin bedroom cikin hanzari jin kiran da Ukhtee take kwaÉ—a min, abakin kofa mukayi kiciÉ“us da ita, fuska na kwaÉ“e ganin tana yi min dariya "Ni gaba É—aya kin firgita ni na É—auka wani abun ne". nayi maganar cikin harshen larabcin da nake É—an tsinta a gurin ta. murmushi tayi tare da ruko hannuna tace "Zo ki gani ga É—an'uwan ki yazo shi yace nayi mishi magana da ke". tayi maganar ne cikin yaren ta da kuma yanayin da zan fahimta, dan yanzu ba laifi nakan fahimci abun da ake faÉ—a da larafci har nakan iya É—an gwamusa wa wajen yin magana da bashi da tsawo mafi sauki. ta janyo ni muka nufi parlour. turus nayi ganin wan da yake zaune a parlour'n su Naseem da Nasmah sun zagaye shi sai zuba masa surutu suke. sai kuma nayi murmushi tare da karasowa cikin parlou'n ina faÉ—in "La Uncle Mahmoud kai ne yaushe ka zo?". dan yanzu kunyar kirashi da sunan sa nake. shima murmushin yayi yana faÉ—in "Ban jima da isowa ba,Naseem yace min kina bacci da zaije ya taso kine nace a'a yabar hajiya ta huta". baki nawashe ina zama kan kujera jin abun da ya faÉ—a nace "Uncle Mahmoud kenan wai hajiya, hajiya kuma". yace "Eh mana hajiya kai, taya za'a taso hajiya a bacci lokacin tashin ta baiyi ba ai dai gara abar hajiya tayi bacci da kyau da kyau". dariya kawai nayi kana nace "Sannu da zuwa ya hanya? yasu Bappa da Inna wuro da Fatu". yace "Hanya lafiya lau, sai dai badaga gida nake ba, amma dai Duk suna Lafiya". Naseem da Nasmah suka mike a jikin sa sukabi bayan Ukhtee aguje sukayi side É—in Mammaa. janyo table É—in da ya É—aura system É—in sa a kai yayi, yajuyo shi ta gabana yana faÉ—in "To hajiya komai fa ya kammala, shiya sa ma na dako musamman tun daga Nigeria zuwa nan na sarnar miki ki kuma ganewa idonki, ba sai an kira ki a waya an sanar miki ba." Ido na kurawa system É—in, ganin bidiyoyi sunata bayyana cikin system É—in, masu É—auke da tamfasa-tamfasan gidaje wane a turai motoci gidajen mai masallatai makarantu haÉ—e da kamfanoni da dai sauran su. cikin tsananin mamaki na dubeshi nace "Wannan fa Uncle Mahmoud?". nayi tambayar ina nuna cikin system É—i. yace "Ah ai kin ki ya kammala wakilci a ka naÉ—a ni domin a kawo miki kiganewa idon ki musamman nataso domin shi". da É—in bin mamaki nakuma kallon hotunan dake bayyana kan system É—in kana na maida dubana gareshi nace "WaÉ—an nan É—in?." yace "Kwarai kuwa sune,nakine sun kammala yanzu ke kawai muke jira ki koma abubbuÉ—e su, sannan kuma ba a gari É—aya akayi su ba a state da dama ne nacikin kasar mu Nigeria, ga jerin sunayin garirruwan da akayi gine ginen a cikin sa". ya daddanna system É—in,sai ga sunayen garuruwan sun bayyana da kuma abubuwan da akayi a kowa ni garin. yace "Kin ga yanzu zaki koma Nigeria a dai-dai dan kullum sai Bappa yayi maga, yanzu ma yace mu dawo tare sai dai ni bagida zan koma ba zan wuce Uganda tare da abokan aiki na, akwai wani abun da zamuje muyi a can". kai na jinjina dan nifa har yau ganin abun nake kamar wasa nace "Him..Him.." kasa magana ma kawai nayi sai Him. nake ta faÉ—a ina kallon ikon Allah,yayin da nakeyi wa Ubangiji buwayi gagara misali tasbihi a can kasar zuciya ta. rufe system É—in yayi kana yace "Kin ga abubuwa yan da suka kammala ko, ko mai masha Allah, yanzu wani suna kike ganin za a sakawa kamfanoni da gidajen mai dai duk sauran kaddarori, wani suna kike ganin ya dace a saka musu, domin idan akaje yin katin gayyata da sanarwa ayi amfani da wannan sunan, da zai zamo shine sunan duka kaddarorin". Shiru nayi yayin da na saka yatsa na guda kan kuma tuna nayi sama da ido na alamun tafiya duniyar tunani, tare da É—an kyafkyafta idon. kana nayi kasa da idon cikin washe baki nace "Yauwa na tuno sunan da nake so a saka masa *HAM'NAS*". nayi kaganar cikin zakuwa ina cigaba da washe baki. yanayin yadda nake maganar sai da ya bashi dariya ya ce "To meye ma'anar *HAM'NAS* É—in kuma". fuskata narufe da tafin hannuna cikin muryar dariya haÉ—e da zakuwar jin yadda na haÉ—a kalmomin suka tafi normal nace "Kaga ma anar sa, HAM sunana ma'ana HAMDAH, NAS kuma Naseem and Nasmah". dariya sosai ya sake yana faÉ—in "Kaga yarin ya mai basira, tabbas wannan suna yayi kuwa ba shakka *HAM'NAS* Co Fitroleum Nigeria Limited *HAM'NAS* Intranational School Of Science And Technology *HAM'NAS* Store Complex *HAM'NAS* Clinics *HAM'NAS* International Hospital, Eh ba shakka lallai sunan yayi *HAM'NAS* Allah ya taimaka yayi jagora". tsabar zakuwa kasa kuma cewa komai nayi sai baki na da yakasa rufuwa..â˜? A ranar da yamma Mahmoud ya wuce Uganda........â˜? Mommyn Twins ce 8/19/22, 10:50 - Ummi Tandama😇: HMD 🅿ï¸?3 Yau juma'a babban rana, ranar da duk kanin al'ummar musulmi suke farin cikin zuwan sa, al'ummar Annabi suna ta kai komo hada-hada da shirye-shiryen tafiya masallaci domin sallar juma'a. da sauri Ummi tafito daga cikin bedroom É—inta sanye da mayafi akanta, fuskarta É—auke da yelwataccen annuri, da ka ganta kasan tana cikin matsanancin farin ciki. da sauri ta nufo bakin kofa, lokacin Fauzan yasako kansa da gudu kaÉ—an yarage yayi karo da Ummi, Ummi ta ce "Kai Fauzan bazaka rika yin abu cikin nutsuwa ba ko." baki ya washe yana waigen bayan sa da faÉ—in "Yau wa Ummi direba yadawo daga masallacin nace masa yafito da mota zai kai ki unguwa." yana maganar yana waigen bayan sa yana wurga hannu alamun zakuwa, sarai Ummi tagane shi so yake ya bita dan tun kan afita a sallah yake fita dubo direba ko yadawo, dan ko masallacin shi baije ba dan ko da tace masa yaje masallaci cewa yayi wai shi a gida yau zaiyi sallah. fita Ummi tayi tana faÉ—in "To naji." bayan ta yabi da sauri yana faÉ—in "Ummi nima zan biki Ummi dan Allah kije dani kin ga wancan Juma'ar da É—ayan wancan juma'ar bakije da ni ba, akwai bashin tafiya unguwa biyu da bake je da ni ba." "Tafican da alla kai ko ina za'aje sai an je da kai kai mata ne, da Nusaiba zamuje kai sai ka jira idan Abba ko Abbu'n ku suka dawo sai kayi musu rakiyar." kafa yashi bubbugawa yana biye da ita a baya tare da faÉ—in "Ummi nikam dai kije dani ina ranar da Nusaiba kuka je." suna isowa tsakar gidan Mamie da Nusaiba suna fitowa, dagudu Fauzan yaje in da suke yaruko hannun Nusaiba da take gyara mayafin ta da ta fito dashi rike a hannu tsabar sauri, jan ta yayi kusa da Mamie yana faÉ—in "Allah yau bazaki je ba dani za aje Mamie rike min ita kar ki sake ta sai nashi mota mun tafi." Mamie tace To cikin muryar dariya ganin yan da ya janyota tana torjewa kamar masu kokawa, Ai ko Mamie na rike ta yajuya a guje yayi gun mota yana dariya da faÉ—in "Yarinya yau badake za aje ba agida zaki zauna." kukan shagwaÉ“a tasake tana jan hannunta dake rike a hannun Mamie tana faÉ—in "Ai wlh dani Ummi zata tafi da kai namace ce sai ka rika bin mata unguwa, Mamie sake ni kuma sai na maka duka." yana isa jikin motar ta zille a hannun Mamie tarufa a guje suka kama rige-rigen shiga mota. tana faÉ—in "Da kai mace ce kuma ai Ummi tace dani zata rika zuwa unguwa." "Allah baki isa ba yaukam dani za a tafi ai sau uku ana tafiya dake unguwa ni ba a tafiya da ni sai naje." yayi maganar yana shigewa cikin motar a guje, itama shigewa tayi ta É—aya barin tana cewa "Bazan taÉ“a zama a gida ba sai dai kai ka zauna." Ummi kam baki ta rike tace "Oh yaran nan sai shegen son yawo duk in da mutum zai je sai kun bishi kamar jakka." dariya Mamie tabisu da shi. da sauri direba yafito yabuÉ—e wa Ummi kofa tashiga, da sauri Nusaiba ta dawo gefen ta yazamo sun sata a tsakiya. sunata yiwa junan su gwalo direba yaja motar suka fita bayan Mamie tayi musu a dawo lafy. koda suka haura titi direba ya juyo ya dubi Ummi yace "Hajiya ina zamu fara zuwa?." yayi tambayar ne dan yasan rana irin ta yau wato ranar ko wata juma'a Ummi tana fita zuwa asibitoci kan titi in da mabarata suke zama dakuma masallaci in da mabarata suke zama, domin basu sadaka a kowace ranar juma'a, dan haka yake da tabbacin wannan fitar ma zuwa guraren zasuyi dan iwar haka suke fita. Ummi tace "Babban masallaci zamu fara zuwa." yace "To Hajiya." nan yajuya akalar tafiyar izuwa babban masallaci. suna isa direba yagyara parking a gefe, Ummi tafito rike da jakarta, yayin da Fauzan da Nusaiba suka rufa mata baya, ta isa in da mabarata suke jere a bakin masallacin, ta buÉ—e jakarta tarika ciro kuÉ—i tana raba musu, tana bin kowa layi-layi tana mika musu sadaka. duk wanda ta mika masa sai ya kwararo mata addu'a da fatan samun biyan bukatun ta na alkhairi ga mahaliccin ta. duk wan da ta bawa idan yayi mata wannan addu'ar sai kaga ta saki wani murmushi tare da fatan tabbatu war hakan acikin zuciyar ta. akasin da da idan sunyi mata addu'ar saboda raunin dake zaune cikin ruciyar ta har sai ya kai ga tayi kukan zuci, tana ji ina ma Ubangiji yakarÉ“i addu'o'in nasu da wanda take hana idanun ta bacci acikin kowani dare, ya kare mata É—iyar ta a duk in da take. gaba É—aya yau É—in nan ta tashi ne cikin farin ciki da jin daÉ—i tana jin kanta cikin wani irin farin ciki mara misaltuwa, wan da ita kanta batasan na mene ne ba. Haka tarika binsu tana raba musu cike da shauki da jin daÉ—in da yagama baibaye zuciyar ta, har sai da ta tabbatar da kowa ya samu, kafin ta koma cikin mota tana jin su suna daÉ—a bin ta da addu'o'i mai kara mata nutsuwa da kwanciyar hankali. daga masallacin kuwa titi-titi suka fara bi in da mabarata ke zama suma tarika mika musu sadaka. kana suka wuce asibiti, har sai da kuÉ—in da ta fito dashi yakare kafin tacewa direba su koma gida.... *(a can kasar Saudiyya cikin masarautar Saudi)* Da sauri nafito daga cikin bathroom ina gyara gashin kaina dana wanke yazubo ya rufe min fuska har bana iya ganin hanya, cikin hanzari na nufi gaban mirror karamar towel in dake rike a hannuna na naÉ—e shi a kaina ina tsane ruwan dake É—iga daga gashina. kana na É—au na'urar dake busar da gashi nabusar da gashin, batare da ya bushi duka ba, nabaza shi ta baya domin iska yakarasa busar da shi. zama ta na gyara na É—au mai nasoma shafawa a jikina. daga cikin mirror nake hango su Ukhtee ita da su Naseem sun sata a tsakiya sai surutu suke zuba mata, suyi da hausa su gwama da larabci abun ka da kwakwalwar yaro sukam tuni suka fini ji da iya mayarwa ma. kai na jinjina a raina nake cewa "Kai waÉ—an nan yara da surutu suke ko surutun wa suka É—auko?." ko É—azu dasuke ta zuwaba Mammaa surutu sai cewa tayi wai ni suka gado, niko ina nake da surutu irin haka. idan kaji maganar su kamar wan da sukayi shekaru huÉ—u wan da ko shekara uku basu cika ba saura wata huÉ—u nan gaba. nayi murmushi kawai tare da girgiza kai, ganin Naseem yajuya fuskarta gareshi in zayi magana Nasmah ma haka. wai su in zasuyi magana ala dole sai mutum na kallon bakin su in bai kallaba sun rika juyo da fuskar shi kenan. wayan Ukhtee ne yashiga kara taÉ—ago wayar tana dubawa kana ta maida duban ta gareni, daga cikin mirror'n muke kallon juna, ganin ta mai da kallon ta kan wayar namike da sauri dan nasan ni ake kiran ganin yan da tayi zuruu tana kaloon wayar tawani langwaÉ“ar da kai, da sauri na isa bakin gadon, ina faÉ—in "Bappa ko?". kai ta gyaÉ—a tare da mika min wayar, na amshi wayar na É—aga kiran tare da kara wayar a kunne. "Assalamualaikum Bappa." daga cikin wayar Bappa yace "Ke HAMDAH me kike yi ne har yanzu baki shirya ba." da sauri nace "Ina kan shiri Bappa yanzu nafito daga wanka ina kan shirin, ina shafa mai ne yanzu." yace "Kada fa ki tsaya wani dogon shafe-shafe kisaka kaya kawai kada jirgi ya tashi ki rasa jirgi kada ki tsaya shiririta irin na rannan." "To Bappa yanzu zan gama". nakashe wayar ina mai jin wani farin ciki. wan nan karon bazan yi wasa ba kamar na wata guda da ya wuce, haka nayita lalawai har jirgi yatafi a bun sa, wannan karon kam ba Bappa kaÉ—ai keson komawa ta ba ni kai na inason komawa kasata, hankali na gaba É—aya yakoma kasata yanzu. ina so najini a cikin ta, ba naganni cikin kasata kaÉ—ai ba, ina so naganni cikin ahalina duk da nasan hakan ba abu mai sauki bane, har idan Abba bai sauka daga fushin da yake dani ba. Mika mata wayar nayi ina kokarin juyawa, wani kiran yakuma shigowa. murmushi nayi ganin Bappa ne yakuma kiran, da safiyar nan kiran sa na shida kenan kan nayi sauri kada jirgi yatafi. "Hello Bappa". nafaÉ—a ina kai wayar kunne na, muryar sa na jiyo yana faÉ—in "Kada ki É“ata lokaci dai kinji ko, kisaka kaya kawai kada ki rasa jirgi ki hanzarta." nace "To Bappa." na sauke wayar na mika mata da sauri na koma gaban mirror, a gaggauce nakarasa shafa mai sai pauda da man baki. na mike da sauri na isa bakin gado in da dama nan nacire kayan da zansaka na aje na É—auka na sa, dan sai da na shirya su Naseem da Nasmah kafin na shiga wanka, shiyasa shirin yayi min sauki. tun da Bappa yakira waya nalura da yanayin Ukhtee gaba ki É—aya yanayin ta ya sauya tayi wani ziruu da ita, kai na kawar dan bana son muhaÉ—a ido da ita, dan yanayin nata zai iya sa jikina ya mutu. cikin hanzari na kammala saka kayana, ina cikin sa kayan ban kai ga gamawa ba Bappa yakuma kira. Nan ma kuma faÉ—in nayi sauri yace, cikin hanzari na kammala saka kayan. Na dubi Naseem da Nasmah ina faÉ—in "Kutashi muje ko." ido Naseem ya kura min yayin da hannayen sa biyu ke dafe da kuma tun sa kana ya ce "Mommy mataiyaci amuje?". Nasmah ma tace "Tayan kaya amuje ko Mommy?." kai na girgiza musu nace "Ba siyan kaya ko masallaci zamu je ba, kasar mu zamu koma can kasar mu in da aka haife mu." ido yaran suka ware suna kallona kana Naseem yakuma cewa "Mommy kasar mu in da aka haife mu?." yy maganar yana zura yatsarsa cikin baki alamun mamaki irin na yara. kai na gyaÉ—a masa tare da ruko hannunsu ina faÉ—in "Kutashi muje." dan nasan idan nabi na surutun su sai mu makara anan har Bappa yakuma kira. Ukhtee kuwa tuni idanunta suka kawo ruwa kan kace me hawaye yafara sauka, hannunta na rike cikin rauni tare da girgiza mata kai dan nima idanuna sun fara tara kwalla. cikin harhaÉ—a larabci nace "Dan Allah Ukhtee kar kisa jikina yayi san yi, baga waya ba zamurika magana ai tafiya ba mutuwa bace ai dai bamu rabu ba tun da akwai waya zamu rika gaisawa, bakin ce zaki zo kasar mu ba?." kai ta gyaÉ—a min alamar Eh nace "To dan Allah kada ki karya min guiwa da tafiyar kizo muje kin ga Bappa sai kira yake." jiki a sanyaye ta mike. koda muka fito parlour sai gani nayi babu akwatin kayan mu in da nafito da shi na ajiye É—azu bayan nagama shirya mana kayan mu. nan Ukhtee take sanar min direba ne yashigo ya É—auka. koda muka fita farfajiyar masarautar, a tsaye jikin mota muka tadda direba da alamu mu yake jira. da sauri na juya na nufi side É—in su Ukhtee dan yiwa Mammaa sallama, narika bin part-part na masarautar ina yi musu sallama duk in da na shiga sai na fito da Æ™walla dan suma da kwallar suke rako ni,haka narika bin side mafi kusa da mu ina yi musu sallama dan idan nace zanbi na nesa da mu sai na kusan sai na É“ata lokaci mai tsawo ban gama ba. daga karshe nashiga can cikin masarautar in da lokacin da mukazo aka canza diamonds É—in nan aciki. direct cikin katafaren parlour wan da aka kawata shi da adon zinari mai matukar É—aukar ido muka shiga, adalin shugaba na zaune a mazaunin sa na alfarma, yayin da Alkur'ani ke gaban sa yana bita cikin nutsuwa. a gaban sa muka rusuna, cikin ladabi nayi masa barka da war haka,kafin nakuma cewa wani abu ya É—aura hannunsa a kai na yana yimin fatan isa kasata lafiya, nayi mamakin yan da yasan abun da ya kawo ni dan ni a zato na bai san da tafiya ta ba. naji daÉ—in addu'o'in da yayi min kwarai da gaske, na mike cikin jin daÉ—i yayin da jikar sa wato Ukhtee ta rufamin baya, bayan itama ta gaishe shi, gaba É—aya cikin parlour'n suka shiga yimin fatar isa gida lafiya ina amsawa da amin har muka fita. a jikin mota na tadda su Mammaa cikin matukar bege kowa sai hawaye yake har sai da suka sa hawaye na ya karu. direba na ganin mu yayi saurin buÉ—e motar yariko hannun su Naseem yasa su cikin motar, rungume juna mukayi da Ukhtee muka saki kuka a tare, gaba ki É—aya gurin hawaye suke babu mai iya rarrashin wani, zame jikina nayi cikin sauri nashige cikin mota, direba yatada motar. motocin da suke jere a gaban mu guda uku sai wasu biyu a bayan mu, motar farko mai tambarin masarautar haÉ—e da jiniya, shi ya fara fita, kafin biyu suka bi bayan sa sai kuma motar da muke ciki. motoci biyu da suke bayan mu suma suka biyo mu, kamar dai ranar da muka shigo masarautar sai gashi yauma a haka muka fita. muna isa airport batare da É“ata lokaci ba muka shige cikin jirgi, nan motocin suka juya. bada jimawa ba jirgin ta É—aga... Bayan wasu Æ´an awanni jirgin mu yasamu sauka cikin yar dar Allah da buwayar sa, cikin babban birnin tarayya Abuja da ke cikin kasata ★NIGERIAâ˜?. bayan saukar jirgen da kamar minti 15 fasinjojin ciki suka fara sauka. da sauri ganin Naseem da Nasmah sun mike kan kace me sun rufa da gudu sunyi bakin kofar fita in da mutane keta sauka, cikin hanzari na rufa musu baya da sauri ina faÉ—in "Kai kutsaya fa kar kuje ku faÉ—i." ai ko da gudu suka fara sauka daga matattakalar jirgin suna dariya. bayan su nabi ina dariya ganin inda suke sauka cap-cap-cap daga matattakalar kamar zasu kefe kasa ina cigaba da faÉ—in. "Zaku faÉ—i fa kutsaya." kan kace me sun sauka kasa, sauri na kara ina sauke kafata kan shinfiÉ—aÉ—É—iyar kasan kasata abun alfahari na Æ™asata Nigeria, naja wani irin numfashi tare da shakar daddaÉ—an iskar dake kaÉ—awa acikin Æ™asata. ganin suna kokarin cigaba da gudun nayi hanzari na ruko su tare da faÉ—in "Idan yaro ya faÉ—i yayi min kuka zan kara masa." baki suka washe cikin kyakyata dariya Naseem yace "Mommy baya mu faÉ—i ba." goshin sa na dungure nace "Zaku faÉ—i mana in zaku faÉ—in zaku sani ne wan nan gudun da kuke ai sai dai kuji ku a kasa kuzo nan ku tsaya." na janyo su gefe guda. Daga can gefe guda da sauri aka buÉ—e wata motar da suke jere É—an nesa da mu, wasu mutane biyu suka fito da sauri suka karaso in da muke, sannu da hanya sukayi min, na amsa ina kokarin janyo su Nasmah mu matsa gefe, daya daga cikin su ya mika min waya, kallon wayar da yake mika min É—in nayi kana na mai da duba na kansa, kai ya É—aya tare da faÉ—in "Ana maga na." ya fada yana kallon kan screen É—in wayar, a hankali na sake Nasmah dake rike a hannun dama ta na amshi wayar, shikuma yayi saurin ruko hannun ta yaÉ—an matsa gefe kaÉ—an in da É—ayan mutu min ke tsaya ya harÉ—e hannu da bakin gilashi a aidon sa, a sannu nakai wayar kunne na tare da yin sallama, daga cikin wayar akace "Barka da isowa kasa Nigeria ki bisu su isa da ke masauki." É—an shiru nayi kamar naso nagane muryar mai maganar, sai kuma na sauke wayar batare da nace komai ba na mika masa wayar. a hankali na soma tafiya suna biye da ni har gurin mota, da sauri É—ayan ya buÉ—e min murfin motar muka shiga in da tuni suka saka jakar mu cikin motar. jere motocin suka fita kamar yan da aka kawo mu airport a can kasar Saudiyya. muna fita daga cikin airport É—in muka É—au hanya, shiru nayi cikin motar ina raba ido cikin Æ™asata yayin da zuciya ta ke kunshe da É—in bin farin cikin gani na cikin Æ™asata, ina jin wani farin ciki tabbas Æ™asata abun alfahari na ne. munyi tafiya mai nisa kafin muka isa wani katafaren hotel, hotel ne irin wan da manyan kusoshin kasa suke sauka a cikin ta... Awani haÉ—eÉ—É—en É—aki aka sauke mu sai da suka rako mu har bakin kofar room É—in kafin suka juya, wan da ke rike da jakar mu kuma yashi ga ya ajiye, kana ya miko min waya yace "Ana magana." na amshi wayar a raina nake faÉ—in "To yanzu kuma ina zai kuma cewa na bisu." a sannu nakara wayar a kunne na sai jin muryar Bappa nayi yana faÉ—in "HAMDAH sannun ku da hanya ya gajiyar hanya." washe baki nayi dajin muryar Bappa da sauri nace "Laaa Bappa mun iso lafiya kalau Bappa kana ina?." nafaÉ—a ina washe baki cike da murna jin muryar Bappa da nayi yace "Kuhuta ku kwanta ku huta sosai ina nan zuwa." nace "To Bappa." na mika masa wayar ina cigaba da washe baki, mutumin ya fita tare da jamin kofa, numfashi na sauke tare da bin É—akin da kallo, na isa bakin gado na zube bakin gado, in da tuni Naseem da Nasmah suka haye gadon sai salle suke. kokarin tuÉ“e kayan jikina nake dan so nake naÉ—an watsa ruwa, naji ana knocking mayafi na naÉ—auka na mayar jikina, na mike na nufi kofar na buÉ—e ma'aikacin hotel É—in nagani tsaye rike da babban tray, baya naja na bashi hanya yashigo ya dire try É—in kan table kana yafita na mai da kofar narufe na murza key. na dawo bakin gadon na tuÉ“e kayana nashige bayi, wanka nayi sosai nafito na tuÉ“e su Naseem suma nayi musu wan kan. bayan na shirya su nima na sauya kaya, kana na zuba mana abinci mukaci. muna gama ci muka koma gado... bayan haka da kamar awa 2 akayi knocking na mike naje na buÉ—e, É—aya daga cikin mutanen da mukazo tare nagani tsaye yace "Madam kun kammala zamu iya tafiya?". kai na gyaÉ—a masa, juyawa nayi dan kiran su Naseem sai ganin su nayi a bayana suna kokarin fita daga É—akin, mutumin ya ruko hannunsu nikuma na koma na É—au mayafi na nabi bayan sa muka fita.. tun daga bakin get É—in da muka iso na fahimci banki muka zo dan gashi a rubuce (First bank) buÉ—e baki nayi a raina nake faÉ—in "To me mukazo yi a banki." bakin na rufe jin yana faÉ—in "Bismillah fito muje ko." sai lokacin na lura ashe ma har sun fita har ya buÉ—e marfin É“arin da nake ban sani ba, a hankali na zuro kafafuna waje na fito. direct cikin bankin muka shige batare datsaida mu ko bincike ba, akasin jama'ar da nagani tsaye bakin bankin an tsaida su an hana su shiga. tun da nashiga cikin bankin aka bani gurin zama ban motsa ba, duk wani cike-cike da kai kawo wasu suke tayi su da wan da mukazo da su, sai dai abun da yakamata ni nayi da kaina shine nake tashi naje nayi, awa 1 da zuwan mu aka kammala komai aka bani ATM, muna fita daga bankin zato na masauki za'a maida mu sai ganin mu nayi a get É—in wani banki, shima kusan mintunan da mukayi a bankin da muka baro mukayi a nan É—in kafin muka kammala, nan ma da ATM É—in bankin muka fita. ina mai jin mamakin kuma zuwan mu wannan bankin. mamaki na bai karu ba sai da nakuma sin tar kaina cikin wata banki, wunin ranar muka kare ta a bin bankuna dan sai da muka je banki biyar kuma duk wan da mukaje da ATM É—in sa muke fita.. sai yamma liss muka dawo masaukin mu, a gajiye na zube bakin gado in da É—aya daga cikin mutanen da muka tafi da su yashigo da su Nasmah, wata laidar dake rike a hannunsa ya mika min yana faÉ—in "Gashi ance na baki." bin laidar nayi da kallo kana namika hannu na amsa shiku yafita, zamata na gyara tare da zuba ATM É—in da suke hannuna kan table É—in gabana. a sannu nashiga buÉ—e laidar dan ganin abun da ke ciki, kwalayen wayoyi ne har guda biyu nagani ciki a sannu na ciro su ina jujjuyasu, rabon da narike waya haka a hannuna a matsayin nawa har na mance, sai kuma cikin hanzari nashiga buÉ—esu dan tun ban ciro su ba wayoyin suka tafi da ni, da sauri na ciro cazar wayoyin duka namike cikin hanzari naje na saka su a cj, ina saka wa kuwa suka nuna min acike suke, da sauri na dawo in da na tashi na kunna wayoyin, ai ko ina kunna wa sai ji kake É—uÉ—ut-É—uÉ—ut alamun shigowar message alert akai-akai. ido na kurawa musu ganin alat ne na kuÉ—i suke ta shigowa, na bankunan da muka buÉ—e É—azu, ido na zubawa sarautar Allah ganin kuÉ—aÉ—en da suke ta shigowa ni bama zan iya kiyaste adadin su ba. sai da naji wayoyin sunbar kara kafin nashiga latsa su, contacts nashiga da sauri sai gani nayi babu number ko É—aya, jiki a sanyaye nake kallon wayar, abu na farko da ya fara zuwar min shine lokacin da Abbu ya siya min waya yasaka min number family na aciki,haka narika bin lambobin Æ´an'uwa na ina kiran su. hawayen da yagangaro kan fuskata na share ina mai jin kewar ahalina, a sannu na mike na isa in da jakata yake na buÉ—e naciro number Ukhtee da ke rubuce a takarda, na saka cikin wayat kana na dannan mata kira, tana É—aga wa dajin nice mai kiran atare muka saki ihun murna. hira mukayi tayi da ita har magriba kafin na mukayi sallama... Kasan cewar ina fashin sallah gado na haye nayi kwanciya ta cike da kewar ahalina daya baibaye ni lokaci guda... washe gari da rana Bappa ya iso Abuja, nayi murna matuka da ganin sa har nake jin wani É“ari na kewar ahalina dana kwana dashi ya yaye da ganin sa. isowar sa ba da jimawa ba muka bar cikin hotel É—in har da kayan mu. wani katafaren gida mai matukar kyau da tsaruwa gida ne babba wan da girmansa yakai ya kawo tsarin sa gwanin burgewa, a bakin ramÉ“asheshen get É—in gidan motar gaban mu ya tsaya, wan da mutanen da suka É—auko mu a airport da wan da muka haÉ—u dasu a banki jiya dakuma wasu karin mutun biyu da yau nafara ganin su, sune acikin motar, motar da muke ciki ke biye da su, sukayi hon, abakin get É—in ramÉ“asheshiyar gidan........â˜? Mommyn Twins ce 8/19/22, 10:51 - Ummi Tandama😇: HMD WASA FARIN GIRKI!!!âœðŸ? _(Book 3)_ 🅿ï¸?4 Asannu a ka wangale tamfatsetsen get É—in gidan, motar gaban mu yakusa ciki, a hankali direban dake jan mu ya danna hancin motar cikin gidan, a tsakiyar farfajiyar gidan duk suka faka motocin, a sannu na zuro kafafuna waje, "Ya ilahi ya littahi". abun da na furta kenan lokacin da na dai-dai ta tsayuwa ta a cikin gidan, bin gidan nashiga yi da ido har ina wai ga gefe da gefe na. gaba É—aya gidan da tsaruwar sa yatafi da ni, tsaruwan gidan yawuci misali komai an tsarashi a inda ya kamata yana ajiye a in da ya dace,gida ne babba mai É—auke da part har huÉ—u, daga gefe can gabar da gidan side ne guda É—aya sai kuma gefe ta hannun dama shima side ne guda sai kuma gefen hagu shima side É—aya, sai dai Æ´an madaidaita ne ba wasu manya ba. daga tsakiyar gidan kuwa wani side ne na musamman wan da yazamo sauran side É—in sun sashi a tsakiya shi kam gini ne mai hawa É—aya babbane ya tsaru iya tsaruwa, daga saman side É—in har kasan sa yaji ado da gilasai masu ban mamaki an kawata shi tamkar a turai,daga kasa kuma an zagaye shi da wasu flaw's masu matukar kyau da É—aukar ido, gaban side É—in wani shinfiÉ—aÉ—É—iyar swimming pool ne wan da aka kawatashi da rubber grass malaye har bakin kofar shiga side É—in. gefe can kuma parking space ne É—auke da lafiyayyun motoci da suka kai guda uhu a cikin sa, daga farin shiga gidan kuma gefe da É—akin mai gadi masallaci ne shin fiÉ—aÉ—e agun, sai kuma É—akuna guda É—ai-É—ai a jere guda uku a gefe da masallacin ta can. Maganar Bappa naji yana faÉ—in "Muje ciki ko HAMDAH." da sauri nadawo daga duniyar kallon gidan dana tafi, da murmushi kan fuskarsa dan ganin yan da na tafi gaba É—aya na shagalta da kallon gidan. na ce "To Bappa". a hankali nabi bayan su side É—in da ke gefe ta hannun dama muka nufa a hankali nake taka kafata ina cigaba da baza ido cikin gidan har muka isa cikin side É—in. masha Allah É—an madaidaicin side É—in ya tsaru matuka. side ne mai É—auke da 3 bedroom ko wanne da banÉ—aki a cikin sa, É—an madaidaicin parlour haÉ—e da dinning da kitchen da komai da komai, an tsara komai yan da yakamata duk wani abun bukata an tanadar babu abun da babu. É—akunan cikin parlour'n muka rika shiga wan da komai akwai hatta gadon É—akunan duk da shinfiÉ—ar su, sunsha lafiyayyun bedsheets. bayan mungama zagaye cikin side É—in gaba É—aya, muka fita É—ayan side É—in dake gefen hagu muka shiga, shima kamar wancan side É—in yaji komai. kowa sai faÉ—in masha Allah yake, nidai kasa magana nayi sai binsu nake inata baiwa idona abinci sabo da gaba É—aya yanayin tsarin gidan yatafi dani. daga nan É—aya side É—in dake can gabar da gidan muka nufa, shima tsaruwan sa da tsarin sa kamar sauran part biyun nan, koda muka fito daga cikin part É—in baki na washe nadubi Bappa dake ta faÉ—in "Kai komai yayi masha Allah komai fa yayi yadda yakamata". baki nakuma washewa ina faÉ—in "Kai wlh Bappa gidan nan Allah yayi kyau kaga fa nan irin wancan can ma irin wancan kai tsarin gidan yayi kyau komai iri É—aya, sai dai kawai kalolin kayan cikin sune daban-daban". dariya Bappa yayi kana yace "Da gaske gidan yayi kyau ko?." "Wlh kuwa Bappa." nafaÉ—a da sauri ina cigaba da washe baki, shima dariyar ya kuma yana girgiza kai kana muka rufawa mutanen baya in da suka nufi wannan kayatacce rantsatstsen babban side É—in nan dake a tsakiyar gidan wan da yazamana da sauran side É—in sun sashi a tsakiya. a hankali muka isa bakin kofar da sauri É—aya daga cikin mutanen ya isa bakin kofar side É—in wan da yake na glass ya É—aura hannunsa gefe kan wasu madannai ya daddanna sai ga glass É—in yafara bada sauti É—an baya yaja kana ya dubeni yace "Bismillah Madam É—an zo ki tsaya a nan." ya nuna min kan step É—in da yasauka akai wan da saika haura kansu kafin ka isa bakin kofar,step ne guda uku, nuna kai na nayi alamar ni?. yace "Eh." a hankali na matso na haura kan step É—in, daga in da yake yamika hannunsa yakuma danna wasu lambobin kana yace na É—aura hannuna kan nan yanuna min wani É—an zagaye da hoton yatsu, a sannu nakai hannuna na dai-dai ta yatsuna kan zanen yastun, nan yafara bada sauri É—it-É—it sai kuma yakuma danna wata lambar data fito mai alamar Okay. nan take kofar tazuge gefe ai ko da sauri na É—aga hannuna. ya juyo yana duba na kana yace "Madam wannan kofar special ne mai amfani da zanen yatsune mutum É—aya ke amfani da shi, sai kuma wancan". yanuna wata kofar dake gefe ya isa gurin muma mukabi bayan sa,ni dai cikin rashin fahimta nake jin sa, yace "Shi wannan common door ne kamar yanda aka sani kowa zai iya amfani da shi." ya murÉ—a handle É—in kofar yabuÉ—e muka shiga ciki. sai gamu mun bayyana cikin wata katafaren parlour ya ilahi ya lilahi, har bansan san da na furta "Kai! amma wannan duk yafisu kyau!". nayi maganar cikin hakikance gaskiyar abun da ke cikin zuciya ta wan da maganar fitowa kawai tayi, Bappa ko karamar dariya yayi tare da jijjiga kai. suma sauran dariya suka bini da shi, nan muka fara kusawa cikin katafaren parlour'n, baki da hanci gaba É—aya na buÉ—e wajen kallon katafare kayataccen parlour'n, faÉ—an tsaruwar sa da misalta tsarin parlour'n ma ba zai misaltuba, yaji kayan alatu da more rayuwar duniya tsaruwan sa ya zarce sauran side É—in da muka shiga babu haÉ—i ko kaÉ—an. bedroom É—in dake cikin parlour'n muka rika shiga É—aya bayan É—aya, bedroom ne zafafa har guda huÉ—u masu É—auke da tsalatsalan bathroom, daga gefe da parlour'n kuwa katon dinning area ne sai kitchen babba a gefe. sama muka hauwa wan da shi kanshi step É—in haurawan sama abun kallo ne domin kuwa shima an kawatashi na musamman. wow masha Allah shima tsarin saman kamar kasan sai dai banbancin kalolin kayan dake cikin su, kalar kujeru da labulayen bedroom and parlour kasan white and ash da É—an ratsin lemon-green. saman shima 4 bedroom ne a cikin sa kalan kayan bedroom and parlour'n kuma white and sky-blu. Antsara komai yadda yakamata sai tashi da sassanyan kamshi mai haÉ—e da kamshin sababbin kaya yake. kai gidan ya haÉ—u fa nidai bakina yakasa rufuwa wajen kallon tsaruwan gidan, bayan mun gama zaga lungu da sako na saman muka gangaro kasa anan muka yada zangon mu cikin parlour'n kasa. Kowa sai yaba kyau da tsaruwar gidan yake, É—aya daga cikin mutanen yadube ni kana yayi gyaran murya sannan ya ce "Madam komai yayi ko? komai ya miki wannan gidan yayi miki? kokuma mu isa wani gidan?." kallon sa nayi cikin rashin faminta sai kuma na maida dubana ga Bappa danaji yana faÉ—in "Duk da dai bataga sauran ba amma ga yanda take ta washe bakin nan ai ba a magana." da sauri nace "Bappa gidan..". bai bari na karasa ba yace "Gidan ki wannan gidan duk girman ta nakine akwai kuma ire-iren su suna nan". ido na waro kamar a mafarki nakejin zancen, "Wannan ya miki?". mutumin yakuma jefo min tambayar, kai nashiga gyaÉ—awa da sauri sai kuma naruko hannun Bappa ina faÉ—in "Eh wlh yayi-yayi Allah Bappa gidan yamin kyau sosaiiiii". Dariya Bappa yayi yace "To sake min hannu kada ki É“ala". ai ko sauran mutanen ma suka rika dariyar ganin yan da nake washe baki ina jijjiga hannun Bappa, Naseem da Nasmah dariya suka rikayi suna tsalle jikin Bappa kamar wan da sun san abun da ake. Mutumin yacigaba da faÉ—in "To masha Allah wannan side É—in shine naki a yanda aka tsara ginin gidan, sauran kuma ke kikasan yan da zakiyi da su, yanzu mu zamu koma mubarki ki huta zamu dawo zuwa gobe, domin sauran baya nai." Sukayi mana sallama suka fita, suna fita, na dubi Bappa ina waro ido nace "Bappa wai da gaske wannan gidana?". Bappa yayi murmushi tare da faÉ—in "DaÉ—ina da ke akwai shirme." hannu nashiga tafawa ina faÉ—in "Kai wlh gidan nan yayi min mugun kyau." ya ce "To sai ki goyashi kuta yawo tun da dai naki ne." ido na waro tare da sa dariya nace "Bappa gidan zan goya?." kanshi ya jinjina yana murmushi. rungume Naseem da Nasmah nayi cikin tsananin farin ciki, sai kuma na sake su. da sauri nace "Bappa ina su Inna wuro da Fatu?." yace "Suna can ruga". nace "Bappa shine bakazo da su ba kace su dawo nan suzo mu zauna da su a nan, kaji Bappa." nafaÉ—a ina jijjiga hannun sa, "Kaji Bappa kace su zo". nakuma faÉ—a ganin yayi shiru bai ce komai ba, yace "A'a HAMDAH su zauna acan zan koma ai nima". ido nakuma warowa da karfi nace "Bappa ni kaÉ—ai za'a barni a wannan gari gudan, da ni kaÉ—ai zan zauna a gidannan ai dani daku zamu zauna." nayi maganar ina nuna cikin parlour'n "Tap Allah bazan iya zama ba dan Allah Bappa kace su dawo nan, wannan gidan ai tsoro zai rika bani ni kaÉ—ai a cikin sa, kaji Bappa?." nafaÉ—a ina bubbuga kafafuna a kasa. "To babu damuwa zasu zo amma ba yanzu ba." na ce "Bappa sai yaushe." ya ce "Bari dai mana a gama Hajiya HAMDAH." dariya yake bani in naji ance Hajiya HAMDAH, ai ko na washe baki, yace "To meyasa bakisa hakorin hajji ba acan?." "Kai Bappa,hhhh to zan sa in na kuma komawa." "Allah ya kai mu ai kamar yanzu ne shekara zata kuma zagowa Allah ya nuna mana cikin masu rai da lafiya." yayi maganar yana mikewa tare da cigaba da faÉ—in "To ni bazanje masallaci gashi ana ta kan kiran sallah, mutumin zo muje muyi sallah". da sauri Naseem ya mike ya roko hannunsa suka fita. Da sauri na mike inata daÉ—a waigen cikin parlour'n inshiga wan É—akin in fita inshiga wancan haka narikayi, daga nan kuma naja hannun Nasmah muka haura sama ina faÉ—in "Bari naje na zaÉ“i bedroom É—in da yafi min." koda muka haura É—akunan duka na shiga kana nazaÉ“i É—aki É—aya, nan cikin bedroom É—in nabuÉ—e bathroom É—in sa na shiga mai girma da tsaruwa kamar É—akin kwana. kayan jikina na tuÉ“e duk da ban jima da yin wanka ba nacika ruwa cikin basin nashige ciki, lumshe idanuna nayi ina jin daÉ—in ruwan na ratsani, najima sosai a ciki kana na wanke jikina da sabulu mai sanyin kamshi da nagani cikin bathroom É—in, sannan nafito. Na sami Nasmah gaban mirror ta É—auki janbaki sai murkawa take a bakin ta. dariya nayi ina faÉ—in "Oh wannan yarin ya ke kam akwai ki da son janbaki". itama baki ta washe tana cigaba da kwaÉ“ula janbakin a bakin ta. da sauri na sauka kasa akwatin kayan mu na janyo nadawo É—akin, a sannu na isa gaban wardrobe dan na shirya kayan ciki, ina buÉ—e wa ido na ware cikin wardrobe É—in ganin kaya ashake a ciki, kama daga kan leshi atamfa material shadda dogayen riguna iri-iri, sai dai ba a É—inke suke ba,a hankali na zaro É—aya daga cikin dogayen riguna wan da suke jere gefe guda masu kyan gaske, na dawo gefen Nasmah na zauna, kana na sauya kayana da dogon rigar nan... Tsabar farincikin da nake jin kaina ciki yau bazai misaltuba, muna zaune har su Bappa suka dawo muka sauko parlour'n kasa muna É—an taÉ“a hira dakuma kallon tv. duban Bappa nayi sai kuma kamar an zabure ni na mike ina faÉ—in "Bappa ina zuwa." sama na haura in da na aje karamar jakata ta hannu na É—auko na buÉ—e jakar naciro wayoyin da jiya aka bani wan da tun da na kunna su nakuma kashewa najefa cikin jakar, dakuma ATM É—in da jiya aka bani su a banki, nadawo in da Bappa suke da sauri nace "Kagani Bappa jiya mutanen nan suka É—auke ni sukayi ta kaini bankuna sukayi ta buÉ—e min account, muna dawowa kuma suka bani waÉ—an nan wayoyin ina kunna su kawai Bappa kaga kuÉ—in da sukayi ta shigowa kawai kuÉ—i sunata shigowa cikin accounts É—in". nayi maganar ina wawwaro idanuna alamun tsantsar mamaki. Murmushi Bappa yayi irin nasu na manya kana yace "HAMDAH kenan ai kuÉ—in kine yake shiga cikin asusun bankin ki, duk wani abun da kikaga yake faruwa duka, duk waÉ—annan mutane dasuke ta zirga-zirga da É—awainiya da ke, duk umurnine daga sama, duk kanin su an É—aurasu ne jagora akan lamarin, shiyasa kikaga duk waÉ—an nan abubuwa suke faruwa duk abun da kikaga sunyi umurnine, sunce min ma gobe idan Allah yakai mu za'a fara kai ki guraren da akayi ayyuka wato guraren kaddarorin ki, kije ki gaggansu gobe za'a fara tafiya shiyasa sukace kihuta yanzu." kai na jinjina alamun gamsuwa, ikon Allah abun kamar a mafarki yake zuwar min. knocking É—in da ake ne yasani mike wa nanufi kofar da nafi zaton tanan ake knocking É—in, na isa jikin kofar na buÉ—e, wani nagani tsaye rike da basket har guda biyu a hannunsa, É—an risinar da kai yayi alamun girmamawa kana ya É—ago yayi min barka da warhaka, na amsa kana yace min order ne daga hotel É—in su akace yakawo nan gidan, kai kawai na girgiza kana nabashi hanya yawuce ciki. dinnig table ya isa ya aje kayan abincin kana yayi mana sallama yafita. muna nan zaune a parlour sai wajen la'asar mukaje mukaci abincin, daga nan Bappa yakuma fita domin zuwa Masallaci shida Naseem. Washegari da safe kamar yan da mutanennan suka ce zasu zo suka iso, suna zaune a parlour nikuma ina ciki domin kimsa su Naseem, ina gama kimsasu muka sauko nan muka É—unguma. yau munsha yawo kaman kaman domin kuwa tundaga unguwar muka fara, wani gida mukaje sakanin sa daÉ—an rata da gidan da muke ciki, sannan muka wuce wasu unguwanni biyu duk kanin su da gidaje É—ai-É—ai, wan da an gama musu komai suna kulle,suka nunnuna min dakuma tabbacin nawa ne, nasha mamaki kwarai daganin manyan gidajen wai kuma a matsayin nawa. daga nan wani tsalelen gidan mai muka je tun daga can nahango ( *HAM'NAS Co Petroleum Nigeria LIMITED* ) wan da aka rubuta da manyan harufa a saman gidan man, tunga nesa zaka iya hango shi É“aro-É“aro. idanuna na lumshe tare dayiwa Ubangiji buwayi gagara misali tasbigi a kasan raina kana na buÉ—e, Mun zaga gidan man na yaba da tsarin sa kwarai yana rufe ne ba'a fara aiki da shi ba, daganan kuma wasu gidajen man mukaje har guda uku duk masu É—auke da ( *HAM'NAS Co Petroleum Nigeria LIMITED* ) daga nan muka kuma zuwa asibitoci suma masu É—auke da sunan ( *HAM'NAS International HOSPITAL* ) suma asibitotin guda uku a gurare daban da ban manyan gaske, sai dai duk a kulle suke anzuba kayan aiki komai da komai acikin su sai dai ba'a fara ai ki da suba. daganan kuma makarantu da kamfanoni muka nufa duk kanin su da tambarin *HAM'NAS* International School Of Science's And Technology, *HAM'NAS Store Complex's su ma duk ba'a fara ai ki da suba. sai kuna masallatai manya guda uku anzuba komai a ciki suma ba'a fara amfani da su ba. Zuwa yanzu kam nidai komai ganin sa nake kamar almara nafara yarda kan cewa komai da gaske ne, sai yamma muka dawo gida, mun dawo a gajiye suke faÉ—a min cewa muhuta nan da kwana uku sai mu fara tafiya guraren kaddarorin dasuke garurruwa nesa da nan, nace to Allah ya kaimu.. Damin Bappa narikayi nace nidai yasa su Inna wuro da Fatu suzo kafin mutafi nan da kwanan ukun, yace a'a abarsu tukun ba yanzu ba, haka dai dole yasa direba yaje ya taho da su dan na tubure a la dole sai an kawo su, ko da direba zaije É—auko su nace yace musu kada suzo da komai, dan cikin side É—in dana matsawa Bappa sai ya zabi É—aya daga cikin side É—in gidan wan da zasu zauna ciki, akwai kaya komai na bukata sai suzo suyi amfani dashi abun da babu sai a karo musu kamar kayan sawa shi da babu a sauran side É—in. hakan kuwa a kayi ranar da su Inna wuro sukazo murna kamar nayi yaya, suma agefen su ba'a magana, na rungume Fatu inata murna, tarika É—aukar su Naseem cikin tsananin farincikin kuma ganin su. a ranar ma Uncle Mahmoud yazo har da matarsa da yaran su, dan su anan Abuja suke gun ai kin sa. nan muka wuni da su wunin ranar yayi min daÉ—i matuka, sai narika jin su tamkar wani É“ari ga ahalina, ganin su yaÉ—an rage min kewa da begen family na. Yau asabar hakan yayi dai-dai da kwanaki ukun da zamuyi tafiyar, da sassafe muka É—auki hanyar suwa Kano, motoci biyu muka tafi dasu motar mu ni da Naseem da Nasmah dakuma Bappa,sai É—aya daga cikin jagororin ke zaune a gefen direba, É—aya motar kuma mutane huÉ—u ne a cikin ta suna gaba muna biye da su. mun isa cikin garin Kano da misalin Æ™arfe 12:30pm sai da muka tsaya mukayi sallah kafin muka nufi inda zamu, gidajen mai muka fara ziyarta kafin asibitoti dakuma kamfanoni. bamufi awa biyu a cikin Kano ba muka É—au hanyar Kaduna a kaduna muka kwana, washegari muka nausa Katsina. Sati biyu muka É—auka muna yawon zuwa garuruwa ganin in da aka zuba ayyuka, masha Allah duk garin da mukaje daga gwamnatin su muke samun tarba da karÉ“a mai muhimmanci, daga karshe muka biyo garin Bauchi, lokacin da motar mu tashiga cikin Bauchi state, tashin hankalin da nashiga bazai misaltuba, wani irin tashin tsikar jiki da sanyi mai matukar shiga jiki su suka ziyarce ni, wani irin É“ari da kakkarwa nasomayi lokaci guda har hakorana suna garuwa da juna, sai kuma wani masifaffen zufa yashiga keto min, hankalin Bappa yayi musifar tashi ganin halin dana shiga lokaci guda, cikin tsananin tashin hankali jin bakon yanayin daya ziyarce ni lokaci guda tamkar Æ™waÆ™walwa ta zata fashe jin wani irin abu mai matukar nauyi da kara ya dankare min a kai, kunnuwa na tamkar ana busa wani irin busa mai matukar kara da firgitar wa, da karfi nakai hannuna na toshe kunnuwana cikin matukar jin azabar dake kokarin tarwasa min rayuwa nashiga faÉ—in "Bappa mu tafi Bappa kace musu kada mu tsaya Bappa mutafi wayyo Allah na". kaina nashiga juyawa da karfi jin yan da zabar da nakeji na karuwa nan take nanimi tunani na na rasa. cikin É—aga murya ganin numfashi nakokarin barin jikina Bappa yace "Direba yi hanzari mufita a cikin garin nan yi maza da sauri!". gudu direba ya kara bai tsaya ba sai da muka fita a garin, gabaki É—aya, hankalin kowa yayi masifar tashi ganin halin da nake ciki, Bappa ko karatun Kur'ani yasoma yanayi yana tofa min, hankali na bai dawo jikina ba har sai da mukabar eriya'n Bauchi gaba É—aya. A hankali narikajin abun da nake jin na sassauta har ya washe. numfashi Bappa ya sauke tare da saida karatun da yake, kai ya girgiza tare da faÉ—in "Kai mutum abin tsoro ne Allah kashiga sakanin nagari da mugu akwai hisabi ranan gobe kiyama". yadubeni da kula yace "Sannu ko HAMDAH". kai na girgiza yace "Me kike ji yanzu?". nuna masa kaina nayi da hannu dan shi ke yimin ciwo sosai. "Zai bari insha Allahu". yayi maganar tare da buÉ—e tafukan hannunsa yasoma karanto Suratul (Khafi) aya goma na farkon surar haÉ—e da ayatul Qursi'yu ya tofa kana yashafamin a kan. cikin yar da da buwayar Allah naji ciwon kan na sauka. Ko da muka shiga jahar plateau state, farkon shiga garin Jos NARKUTA. wasu zafafan kwalla ne suka gangaro kan fuskata tuno da Mama mai awara, da sauri nayi yinkurin yin magana a tsaya amma abun mamaki sai naji harshe na yayi min mugun nauyi gaba É—aya jikina ya sake babu alamar karfi tattare da ni, abun da na fahimta tun lokacin da nayiwa Bappa maga shigar mu Bauchi zan kuma wata maganar naji na kasa, har kuma yanzu ina jin yanayin... da daddare muka shiga Abuja, da kyar da taimakon Bappa na iya sauka cikin mota muka shiga ciki. Inna wuro ta firgita da ganin yanayi na, ko da Bappa yayi mata bayanin abun da ya faru, hankalin ta yayi masifar tashi, yace ta taimaka min naje na kwanta, shikuma yafita can ya dawo da É—an karamin Æ™warya da magani a ciki yabawa Inna wuro yace "Kibata tasha babu komai insha Allah zata ware garin ne kwatakwata basa so tashiga sai dai tayi nesa da shi sun mance cewa Allah baya bacci". Inna wuro tace "Ikon Allah wannan irin shiga sakani sai sakayyar Ubangiji". ko da Inna wuro ta bani maganin inasha bada jimawaba bacci yaÉ—auke ni, ranar a kaina ta kwana, Fatu kuma tana tare da su Naseem a É—aya É—akin dake kusa da nawa. washegari kuwa cikin yarda da buwayar Allah namike garau... muna tare a parlour ni Inna wuro Fatu dan har lokacin basu koma side É—in suba, labarin garuruwan da mukajejje narika basu ina washe baki da faÉ—in "Allah Inna wuro bakuga abubuwan yan da sukayi kyau ba kai har da garin da ban taÉ“a zuwa ba". nayi maganar ina washe baki, dariya suka rika min, nan Bappa yashigo ganin jikina shima yazauna mukayi ta hira.... bayan kwana biyu Mutane biyu daga cikin jagororin nan suka zo su da wasu mata guda biyar sukace na zama a cikin su wan da zasu rika yi min ai ki, mata ne irin wan da suke karkashin paundation, irin waÉ—an da mazajensu suka sake su dakuma wan da mazajensu suka rasu, akan É—auke su ai ki irin gidajen masu kuÉ—i É—in nan, a cikin su na zaÉ“i guda uku dasukafi kwanciya min a rai, kana nace zan gwada ai ki da su. É—aya na É—auke ta a matsayin mai kula da su Nasmah dakuma kula da tsaftar side É—in, na biyun kuma mai girka abibci, sai kuma É—ayar na turawasu Inna wuro ita zata rika kula da tsaftar side É—in su dakuma girkin su. nan suka kuma gabatar min da masu maza wan da nazo nasame su a cikin gidan, direba sai mai baiwa fulawa ruwa shi zai rika wanke mota, sai mai gadi dakuma mai kula da tsaftar farfajiyar gidan gaba É—aya. mun zauna da su na É—an wani lokaci na fahimci mutane ne masu kirki da rukon amana. Haka rayuwa tacigaba da tafi, tuni akayi bikin buÉ—e masana'antu da masallatan nan manyan shuwagabannin Nigeria sun halacci torurrukan sun kuma bada gudummawar su kwarai da gaske wajen ganin an É—ibi ma'aikata masu inganci. Bayan wani lokaci Tuni aka damkamin ragamar duk wasu kaddarori na ni nake bada umurnin ayi da kuma kar ayi, har kuma yanzu muna tare da jagororin nan su suke sanya ido kan ganin komai yatafi dai-dai. tuni nasa aka baiwa Fatu uniform a É—aya daga cikin makarantu na, dan dama acan rugar ma tana karatun ta tacigaba a nan. Zaune nake a parlour ina dudduba jerin sunayen mata da matasan da nasa a É—iba, a karkashin paudasion É—ina domin basu tallafin wasu kuÉ—aÉ—en da zai jamusu jari domin dogaro da kai na tura da kuÉ—aÉ—en tallafin izuwa asusun *HAM'NAS* paudasion. a hankali na mike tsaye tare da yin mika haÉ—e da salati, wayoyina na tattara haÉ—e da sabuwar system É—ina, na haura sama, kan bedside na ajiye su kana na haye gado dan bacci nake ji, ina so nayi baccin kafin su Naseem su shigo dan suna can side É—in su Bappa. har na kwanta na tuna da akwai maganar da nake so muyi da Bappa kan wani Company na murza karfe da ake gina shi a Lagos, mikewa nayi na fita dan ina so muje ziyarar gani da ido acikin satin nan. da gudu Nasmah ta shigo tana faÉ—in "Mommy kin ga Naseem ko jai camin jiji". Naseem shima dagudun yashigo yana binta da abun yana dariya, Fatu na biye da su tana dariya da faÉ—in "Naseem kabari kar ka sa mata". da sauri nakarasa sauka kan step na rungumo Nasmah dake falfala gudu kamar zata kife kasa nace "K.......!â˜? Mommyn Twins ce 8/19/22, 10:54 - Ummi Tandama😇: HMD WASA FARIN GIRKI!!!âœðŸ? _(Book 3)_ 🅿ï¸?4 Asannu a ka wangale tamfatsetsen get É—in gidan, motar gaban mu yakusa ciki, a hankali direban dake jan mu ya danna hancin motar cikin gidan, a tsakiyar farfajiyar gidan duk suka faka motocin, a sannu na zuro kafafuna waje, "Ya ilahi ya littahi". abun da na furta kenan lokacin da na dai-dai ta tsayuwa ta a cikin gidan, bin gidan nashiga yi da ido har ina wai ga gefe da gefe na. gaba É—aya gidan da tsaruwar sa yatafi da ni, tsaruwan gidan yawuci misali komai an tsarashi a inda ya kamata yana ajiye a in da ya dace,gida ne babba mai É—auke da part har huÉ—u, daga gefe can gabar da gidan side ne guda É—aya sai kuma gefe ta hannun dama shima side ne guda sai kuma gefen hagu shima side É—aya, sai dai Æ´an madaidaita ne ba wasu manya ba. daga tsakiyar gidan kuwa wani side ne na musamman wan da yazamo sauran side É—in sun sashi a tsakiya shi kam gini ne mai hawa É—aya babbane ya tsaru iya tsaruwa, daga saman side É—in har kasan sa yaji ado da gilasai masu ban mamaki an kawata shi tamkar a turai,daga kasa kuma an zagaye shi da wasu flaw's masu matukar kyau da É—aukar ido, gaban side É—in wani shinfiÉ—aÉ—É—iyar swimming pool ne wan da aka kawatashi da rubber grass malaye har bakin kofar shiga side É—in. gefe can kuma parking space ne É—auke da lafiyayyun motoci da suka kai guda uhu a cikin sa, daga farin shiga gidan kuma gefe da É—akin mai gadi masallaci ne shin fiÉ—aÉ—e agun, sai kuma É—akuna guda É—ai-É—ai a jere guda uku a gefe da masallacin ta can. Maganar Bappa naji yana faÉ—in "Muje ciki ko HAMDAH." da sauri nadawo daga duniyar kallon gidan dana tafi, da murmushi kan fuskarsa dan ganin yan da na tafi gaba É—aya na shagalta da kallon gidan. na ce "To Bappa". a hankali nabi bayan su side É—in da ke gefe ta hannun dama muka nufa a hankali nake taka kafata ina cigaba da baza ido cikin gidan har muka isa cikin side É—in. masha Allah É—an madaidaicin side É—in ya tsaru matuka. side ne mai É—auke da 3 bedroom ko wanne da banÉ—aki a cikin sa, É—an madaidaicin parlour haÉ—e da dinning da kitchen da komai da komai, an tsara komai yan da yakamata duk wani abun bukata an tanadar babu abun da babu. É—akunan cikin parlour'n muka rika shiga wan da komai akwai hatta gadon É—akunan duk da shinfiÉ—ar su, sunsha lafiyayyun bedsheets. bayan mungama zagaye cikin side É—in gaba É—aya, muka fita É—ayan side É—in dake gefen hagu muka shiga, shima kamar wancan side É—in yaji komai. kowa sai faÉ—in masha Allah yake, nidai kasa magana nayi sai binsu nake inata baiwa idona abinci sabo da gaba É—aya yanayin tsarin gidan yatafi dani. daga nan É—aya side É—in dake can gabar da gidan muka nufa, shima tsaruwan sa da tsarin sa kamar sauran part biyun nan, koda muka fito daga cikin part É—in baki na washe nadubi Bappa dake ta faÉ—in "Kai komai yayi masha Allah komai fa yayi yadda yakamata". baki nakuma washewa ina faÉ—in "Kai wlh Bappa gidan nan Allah yayi kyau kaga fa nan irin wancan can ma irin wancan kai tsarin gidan yayi kyau komai iri É—aya, sai dai kawai kalolin kayan cikin sune daban-daban". dariya Bappa yayi kana yace "Da gaske gidan yayi kyau ko?." "Wlh kuwa Bappa." nafaÉ—a da sauri ina cigaba da washe baki, shima dariyar ya kuma yana girgiza kai kana muka rufawa mutanen baya in da suka nufi wannan kayatacce rantsatstsen babban side É—in nan dake a tsakiyar gidan wan da yazamana da sauran side É—in sun sashi a tsakiya. a hankali muka isa bakin kofar da sauri É—aya daga cikin mutanen ya isa bakin kofar side É—in wan da yake na glass ya É—aura hannunsa gefe kan wasu madannai ya daddanna sai ga glass É—in yafara bada sauti É—an baya yaja kana ya dubeni yace "Bismillah Madam É—an zo ki tsaya a nan." ya nuna min kan step É—in da yasauka akai wan da saika haura kansu kafin ka isa bakin kofar,step ne guda uku, nuna kai na nayi alamar ni?. yace "Eh." a hankali na matso na haura kan step É—in, daga in da yake yamika hannunsa yakuma danna wasu lambobin kana yace na É—aura hannuna kan nan yanuna min wani É—an zagaye da hoton yatsu, a sannu nakai hannuna na dai-dai ta yatsuna kan zanen yastun, nan yafara bada sauri É—it-É—it sai kuma yakuma danna wata lambar data fito mai alamar Okay. nan take kofar tazuge gefe ai ko da sauri na É—aga hannuna. ya juyo yana duba na kana yace "Madam wannan kofar special ne mai amfani da zanen yatsune mutum É—aya ke amfani da shi, sai kuma wancan". yanuna wata kofar dake gefe ya isa gurin muma mukabi bayan sa,ni dai cikin rashin fahimta nake jin sa, yace "Shi wannan common door ne kamar yanda aka sani kowa zai iya amfani da shi." ya murÉ—a handle É—in kofar yabuÉ—e muka shiga ciki. sai gamu mun bayyana cikin wata katafaren parlour ya ilahi ya lilahi, har bansan san da na furta "Kai! amma wannan duk yafisu kyau!". nayi maganar cikin hakikance gaskiyar abun da ke cikin zuciya ta wan da maganar fitowa kawai tayi, Bappa ko karamar dariya yayi tare da jijjiga kai. suma sauran dariya suka bini da shi, nan muka fara kusawa cikin katafaren parlour'n, baki da hanci gaba É—aya na buÉ—e wajen kallon katafare kayataccen parlour'n, faÉ—an tsaruwar sa da misalta tsarin parlour'n ma ba zai misaltuba, yaji kayan alatu da more rayuwar duniya tsaruwan sa ya zarce sauran side É—in da muka shiga babu haÉ—i ko kaÉ—an. bedroom É—in dake cikin parlour'n muka rika shiga É—aya bayan É—aya, bedroom ne zafafa har guda huÉ—u masu É—auke da tsalatsalan bathroom, daga gefe da parlour'n kuwa katon dinning area ne sai kitchen babba a gefe. sama muka hauwa wan da shi kanshi step É—in haurawan sama abun kallo ne domin kuwa shima an kawatashi na musamman. wow masha Allah shima tsarin saman kamar kasan sai dai banbancin kalolin kayan dake cikin su, kalar kujeru da labulayen bedroom and parlour kasan white and ash da É—an ratsin lemon-green. saman shima 4 bedroom ne a cikin sa kalan kayan bedroom and parlour'n kuma white and sky-blu. Antsara komai yadda yakamata sai tashi da sassanyan kamshi mai haÉ—e da kamshin sababbin kaya yake. kai gidan ya haÉ—u fa nidai bakina yakasa rufuwa wajen kallon tsaruwan gidan, bayan mun gama zaga lungu da sako na saman muka gangaro kasa anan muka yada zangon mu cikin parlour'n kasa. Kowa sai yaba kyau da tsaruwar gidan yake, É—aya daga cikin mutanen yadube ni kana yayi gyaran murya sannan ya ce "Madam komai yayi ko? komai ya miki wannan gidan yayi miki? kokuma mu isa wani gidan?." kallon sa nayi cikin rashin faminta sai kuma na maida dubana ga Bappa danaji yana faÉ—in "Duk da dai bataga sauran ba amma ga yanda take ta washe bakin nan ai ba a magana." da sauri nace "Bappa gidan..". bai bari na karasa ba yace "Gidan ki wannan gidan duk girman ta nakine akwai kuma ire-iren su suna nan". ido na waro kamar a mafarki nakejin zancen, "Wannan ya miki?". mutumin yakuma jefo min tambayar, kai nashiga gyaÉ—awa da sauri sai kuma naruko hannun Bappa ina faÉ—in "Eh wlh yayi-yayi Allah Bappa gidan yamin kyau sosaiiiii". Dariya Bappa yayi yace "To sake min hannu kada ki É“ala". ai ko sauran mutanen ma suka rika dariyar ganin yan da nake washe baki ina jijjiga hannun Bappa, Naseem da Nasmah dariya suka rikayi suna tsalle jikin Bappa kamar wan da sun san abun da ake. Mutumin yacigaba da faÉ—in "To masha Allah wannan side É—in shine naki a yanda aka tsara ginin gidan, sauran kuma ke kikasan yan da zakiyi da su, yanzu mu zamu koma mubarki ki huta zamu dawo zuwa gobe, domin sauran baya nai." Sukayi mana sallama suka fita, suna fita, na dubi Bappa ina waro ido nace "Bappa wai da gaske wannan gidana?". Bappa yayi murmushi tare da faÉ—in "DaÉ—ina da ke akwai shirme." hannu nashiga tafawa ina faÉ—in "Kai wlh gidan nan yayi min mugun kyau." ya ce "To sai ki goyashi kuta yawo tun da dai naki ne." ido na waro tare da sa dariya nace "Bappa gidan zan goya?." kanshi ya jinjina yana murmushi. rungume Naseem da Nasmah nayi cikin tsananin farin ciki, sai kuma na sake su. da sauri nace "Bappa ina su Inna wuro da Fatu?." yace "Suna can ruga". nace "Bappa shine bakazo da su ba kace su dawo nan suzo mu zauna da su a nan, kaji Bappa." nafaÉ—a ina jijjiga hannun sa, "Kaji Bappa kace su zo". nakuma faÉ—a ganin yayi shiru bai ce komai ba, yace "A'a HAMDAH su zauna acan zan koma ai nima". ido nakuma warowa da karfi nace "Bappa ni kaÉ—ai za'a barni a wannan gari gudan, da ni kaÉ—ai zan zauna a gidannan ai dani daku zamu zauna." nayi maganar ina nuna cikin parlour'n "Tap Allah bazan iya zama ba dan Allah Bappa kace su dawo nan, wannan gidan ai tsoro zai rika bani ni kaÉ—ai a cikin sa, kaji Bappa?." nafaÉ—a ina bubbuga kafafuna a kasa. "To babu damuwa zasu zo amma ba yanzu ba." na ce "Bappa sai yaushe." ya ce "Bari dai mana a gama Hajiya HAMDAH." dariya yake bani in naji ance Hajiya HAMDAH, ai ko na washe baki, yace "To meyasa bakisa hakorin hajji ba acan?." "Kai Bappa,hhhh to zan sa in na kuma komawa." "Allah ya kai mu ai kamar yanzu ne shekara zata kuma zagowa Allah ya nuna mana cikin masu rai da lafiya." yayi maganar yana mikewa tare da cigaba da faÉ—in "To ni bazanje masallaci gashi ana ta kan kiran sallah, mutumin zo muje muyi sallah". da sauri Naseem ya mike ya roko hannunsa suka fita. Da sauri na mike inata daÉ—a waigen cikin parlour'n inshiga wan É—akin in fita inshiga wancan haka narikayi, daga nan kuma naja hannun Nasmah muka haura sama ina faÉ—in "Bari naje na zaÉ“i bedroom É—in da yafi min." koda muka haura É—akunan duka na shiga kana nazaÉ“i É—aki É—aya, nan cikin bedroom É—in nabuÉ—e bathroom É—in sa na shiga mai girma da tsaruwa kamar É—akin kwana. kayan jikina na tuÉ“e duk da ban jima da yin wanka ba nacika ruwa cikin basin nashige ciki, lumshe idanuna nayi ina jin daÉ—in ruwan na ratsani, najima sosai a ciki kana na wanke jikina da sabulu mai sanyin kamshi da nagani cikin bathroom É—in, sannan nafito. Na sami Nasmah gaban mirror ta É—auki janbaki sai murkawa take a bakin ta. dariya nayi ina faÉ—in "Oh wannan yarin ya ke kam akwai ki da son janbaki". itama baki ta washe tana cigaba da kwaÉ“ula janbakin a bakin ta. da sauri na sauka kasa akwatin kayan mu na janyo nadawo É—akin, a sannu na isa gaban wardrobe dan na shirya kayan ciki, ina buÉ—e wa ido na ware cikin wardrobe É—in ganin kaya ashake a ciki, kama daga kan leshi atamfa material shadda dogayen riguna iri-iri, sai dai ba a É—inke suke ba,a hankali na zaro É—aya daga cikin dogayen riguna wan da suke jere gefe guda masu kyan gaske, na dawo gefen Nasmah na zauna, kana na sauya kayana da dogon rigar nan... Tsabar farincikin da nake jin kaina ciki yau bazai misaltuba, muna zaune har su Bappa suka dawo muka sauko parlour'n kasa muna É—an taÉ“a hira dakuma kallon tv. duban Bappa nayi sai kuma kamar an zabure ni na mike ina faÉ—in "Bappa ina zuwa." sama na haura in da na aje karamar jakata ta hannu na É—auko na buÉ—e jakar naciro wayoyin da jiya aka bani wan da tun da na kunna su nakuma kashewa najefa cikin jakar, dakuma ATM É—in da jiya aka bani su a banki, nadawo in da Bappa suke da sauri nace "Kagani Bappa jiya mutanen nan suka É—auke ni sukayi ta kaini bankuna sukayi ta buÉ—e min account, muna dawowa kuma suka bani waÉ—an nan wayoyin ina kunna su kawai Bappa kaga kuÉ—in da sukayi ta shigowa kawai kuÉ—i sunata shigowa cikin accounts É—in". nayi maganar ina wawwaro idanuna alamun tsantsar mamaki. Murmushi Bappa yayi irin nasu na manya kana yace "HAMDAH kenan ai kuÉ—in kine yake shiga cikin asusun bankin ki, duk wani abun da kikaga yake faruwa duka, duk waÉ—annan mutane dasuke ta zirga-zirga da É—awainiya da ke, duk umurnine daga sama, duk kanin su an É—aurasu ne jagora akan lamarin, shiyasa kikaga duk waÉ—an nan abubuwa suke faruwa duk abun da kikaga sunyi umurnine, sunce min ma gobe idan Allah yakai mu za'a fara kai ki guraren da akayi ayyuka wato guraren kaddarorin ki, kije ki gaggansu gobe za'a fara tafiya shiyasa sukace kihuta yanzu." kai na jinjina alamun gamsuwa, ikon Allah abun kamar a mafarki yake zuwar min. knocking É—in da ake ne yasani mike wa nanufi kofar da nafi zaton tanan ake knocking É—in, na isa jikin kofar na buÉ—e, wani nagani tsaye rike da basket har guda biyu a hannunsa, É—an risinar da kai yayi alamun girmamawa kana ya É—ago yayi min barka da warhaka, na amsa kana yace min order ne daga hotel É—in su akace yakawo nan gidan, kai kawai na girgiza kana nabashi hanya yawuce ciki. dinnig table ya isa ya aje kayan abincin kana yayi mana sallama yafita. muna nan zaune a parlour sai wajen la'asar mukaje mukaci abincin, daga nan Bappa yakuma fita domin zuwa Masallaci shida Naseem. Washegari da safe kamar yan da mutanennan suka ce zasu zo suka iso, suna zaune a parlour nikuma ina ciki domin kimsa su Naseem, ina gama kimsasu muka sauko nan muka É—unguma. yau munsha yawo kaman kaman domin kuwa tundaga unguwar muka fara, wani gida mukaje sakanin sa daÉ—an rata da gidan da muke ciki, sannan muka wuce wasu unguwanni biyu duk kanin su da gidaje É—ai-É—ai, wan da an gama musu komai suna kulle,suka nunnuna min dakuma tabbacin nawa ne, nasha mamaki kwarai daganin manyan gidajen wai kuma a matsayin nawa. daga nan wani tsalelen gidan mai muka je tun daga can nahango ( *HAM'NAS Co Petroleum Nigeria LIMITED* ) wan da aka rubuta da manyan harufa a saman gidan man, tunga nesa zaka iya hango shi É“aro-É“aro. idanuna na lumshe tare dayiwa Ubangiji buwayi gagara misali tasbigi a kasan raina kana na buÉ—e, Mun zaga gidan man na yaba da tsarin sa kwarai yana rufe ne ba'a fara aiki da shi ba, daganan kuma wasu gidajen man mukaje har guda uku duk masu É—auke da ( *HAM'NAS Co Petroleum Nigeria LIMITED* ) daga nan muka kuma zuwa asibitoci suma masu É—auke da sunan ( *HAM'NAS International HOSPITAL* ) suma asibitotin guda uku a gurare daban da ban manyan gaske, sai dai duk a kulle suke anzuba kayan aiki komai da komai acikin su sai dai ba'a fara ai ki da suba. daganan kuma makarantu da kamfanoni muka nufa duk kanin su da tambarin *HAM'NAS* International School Of Science's And Technology, *HAM'NAS Store Complex's su ma duk ba'a fara ai ki da suba. sai kuna masallatai manya guda uku anzuba komai a ciki suma ba'a fara amfani da su ba. Zuwa yanzu kam nidai komai ganin sa nake kamar almara nafara yarda kan cewa komai da gaske ne, sai yamma muka dawo gida, mun dawo a gajiye suke faÉ—a min cewa muhuta nan da kwana uku sai mu fara tafiya guraren kaddarorin dasuke garurruwa nesa da nan, nace to Allah ya kaimu.. Damin Bappa narikayi nace nidai yasa su Inna wuro da Fatu suzo kafin mutafi nan da kwanan ukun, yace a'a abarsu tukun ba yanzu ba, haka dai dole yasa direba yaje ya taho da su dan na tubure a la dole sai an kawo su, ko da direba zaije É—auko su nace yace musu kada suzo da komai, dan cikin side É—in dana matsawa Bappa sai ya zabi É—aya daga cikin side É—in gidan wan da zasu zauna ciki, akwai kaya komai na bukata sai suzo suyi amfani dashi abun da babu sai a karo musu kamar kayan sawa shi da babu a sauran side É—in. hakan kuwa a kayi ranar da su Inna wuro sukazo murna kamar nayi yaya, suma agefen su ba'a magana, na rungume Fatu inata murna, tarika É—aukar su Naseem cikin tsananin farincikin kuma ganin su. a ranar ma Uncle Mahmoud yazo har da matarsa da yaran su, dan su anan Abuja suke gun ai kin sa. nan muka wuni da su wunin ranar yayi min daÉ—i matuka, sai narika jin su tamkar wani É“ari ga ahalina, ganin su yaÉ—an rage min kewa da begen family na. Yau asabar hakan yayi dai-dai da kwanaki ukun da zamuyi tafiyar, da sassafe muka É—auki hanyar suwa Kano, motoci biyu muka tafi dasu motar mu ni da Naseem da Nasmah dakuma Bappa,sai É—aya daga cikin jagororin ke zaune a gefen direba, É—aya motar kuma mutane huÉ—u ne a cikin ta suna gaba muna biye da su. mun isa cikin garin Kano da misalin Æ™arfe 12:30pm sai da muka tsaya mukayi sallah kafin muka nufi inda zamu, gidajen mai muka fara ziyarta kafin asibitoti dakuma kamfanoni. bamufi awa biyu a cikin Kano ba muka É—au hanyar Kaduna a kaduna muka kwana, washegari muka nausa Katsina. Sati biyu muka É—auka muna yawon zuwa garuruwa ganin in da aka zuba ayyuka, masha Allah duk garin da mukaje daga gwamnatin su muke samun tarba da karÉ“a mai muhimmanci, daga karshe muka biyo garin Bauchi, lokacin da motar mu tashiga cikin Bauchi state, tashin hankalin da nashiga bazai misaltuba, wani irin tashin tsikar jiki da sanyi mai matukar shiga jiki su suka ziyarce ni, wani irin É“ari da kakkarwa nasomayi lokaci guda har hakorana suna garuwa da juna, sai kuma wani masifaffen zufa yashiga keto min, hankalin Bappa yayi musifar tashi ganin halin dana shiga lokaci guda, cikin tsananin tashin hankali jin bakon yanayin daya ziyarce ni lokaci guda tamkar Æ™waÆ™walwa ta zata fashe jin wani irin abu mai matukar nauyi da kara ya dankare min a kai, kunnuwa na tamkar ana busa wani irin busa mai matukar kara da firgitar wa, da karfi nakai hannuna na toshe kunnuwana cikin matukar jin azabar dake kokarin tarwasa min rayuwa nashiga faÉ—in "Bappa mu tafi Bappa kace musu kada mu tsaya Bappa mutafi wayyo Allah na". kaina nashiga juyawa da karfi jin yan da zabar da nakeji na karuwa nan take nanimi tunani na na rasa. cikin É—aga murya ganin numfashi nakokarin barin jikina Bappa yace "Direba yi hanzari mufita a cikin garin nan yi maza da sauri!". gudu direba ya kara bai tsaya ba sai da muka fita a garin, gabaki É—aya, hankalin kowa yayi masifar tashi ganin halin da nake ciki, Bappa ko karatun Kur'ani yasoma yanayi yana tofa min, hankali na bai dawo jikina ba har sai da mukabar eriya'n Bauchi gaba É—aya. A hankali narikajin abun da nake jin na sassauta har ya washe. numfashi Bappa ya sauke tare da saida karatun da yake, kai ya girgiza tare da faÉ—in "Kai mutum abin tsoro ne Allah kashiga sakanin nagari da mugu akwai hisabi ranan gobe kiyama". yadubeni da kula yace "Sannu ko HAMDAH". kai na girgiza yace "Me kike ji yanzu?". nuna masa kaina nayi da hannu dan shi ke yimin ciwo sosai. "Zai bari insha Allahu". yayi maganar tare da buÉ—e tafukan hannunsa yasoma karanto Suratul (Khafi) aya goma na farkon surar haÉ—e da ayatul Qursi'yu ya tofa kana yashafamin a kan. cikin yar da da buwayar Allah naji ciwon kan na sauka. Ko da muka shiga jahar plateau state, farkon shiga garin Jos NARKUTA. wasu zafafan kwalla ne suka gangaro kan fuskata tuno da Mama mai awara, da sauri nayi yinkurin yin magana a tsaya amma abun mamaki sai naji harshe na yayi min mugun nauyi gaba É—aya jikina ya sake babu alamar karfi tattare da ni, abun da na fahimta tun lokacin da nayiwa Bappa maga shigar mu Bauchi zan kuma wata maganar naji na kasa, har kuma yanzu ina jin yanayin... da daddare muka shiga Abuja, da kyar da taimakon Bappa na iya sauka cikin mota muka shiga ciki. Inna wuro ta firgita da ganin yanayi na, ko da Bappa yayi mata bayanin abun da ya faru, hankalin ta yayi masifar tashi, yace ta taimaka min naje na kwanta, shikuma yafita can ya dawo da É—an karamin Æ™warya da magani a ciki yabawa Inna wuro yace "Kibata tasha babu komai insha Allah zata ware garin ne kwatakwata basa so tashiga sai dai tayi nesa da shi sun mance cewa Allah baya bacci". Inna wuro tace "Ikon Allah wannan irin shiga sakani sai sakayyar Ubangiji". ko da Inna wuro ta bani maganin inasha bada jimawaba bacci yaÉ—auke ni, ranar a kaina ta kwana, Fatu kuma tana tare da su Naseem a É—aya É—akin dake kusa da nawa. washegari kuwa cikin yarda da buwayar Allah namike garau... muna tare a parlour ni Inna wuro Fatu dan har lokacin basu koma side É—in suba, labarin garuruwan da mukajejje narika basu ina washe baki da faÉ—in "Allah Inna wuro bakuga abubuwan yan da sukayi kyau ba kai har da garin da ban taÉ“a zuwa ba". nayi maganar ina washe baki, dariya suka rika min, nan Bappa yashigo ganin jikina shima yazauna mukayi ta hira.... bayan kwana biyu Mutane biyu daga cikin jagororin nan suka zo su da wasu mata guda biyar sukace na zama a cikin su wan da zasu rika yi min ai ki, mata ne irin wan da suke karkashin paundation, irin waÉ—an da mazajensu suka sake su dakuma wan da mazajensu suka rasu, akan É—auke su ai ki irin gidajen masu kuÉ—i É—in nan, a cikin su na zaÉ“i guda uku dasukafi kwanciya min a rai, kana nace zan gwada ai ki da su. É—aya na É—auke ta a matsayin mai kula da su Nasmah dakuma kula da tsaftar side É—in, na biyun kuma mai girka abibci, sai kuma É—ayar na turawasu Inna wuro ita zata rika kula da tsaftar side É—in su dakuma girkin su. nan suka kuma gabatar min da masu maza wan da nazo nasame su a cikin gidan, direba sai mai baiwa fulawa ruwa shi zai rika wanke mota, sai mai gadi dakuma mai kula da tsaftar farfajiyar gidan gaba É—aya. mun zauna da su na É—an wani lokaci na fahimci mutane ne masu kirki da rukon amana. Haka rayuwa tacigaba da tafi, tuni akayi bikin buÉ—e masana'antu da masallatan nan manyan shuwagabannin Nigeria sun halacci torurrukan sun kuma bada gudummawar su kwarai da gaske wajen ganin an É—ibi ma'aikata masu inganci. Bayan wani lokaci Tuni aka damkamin ragamar duk wasu kaddarori na ni nake bada umurnin ayi da kuma kar ayi, har kuma yanzu muna tare da jagororin nan su suke sanya ido kan ganin komai yatafi dai-dai. tuni nasa aka baiwa Fatu uniform a É—aya daga cikin makarantu na, dan dama acan rugar ma tana karatun ta tacigaba a nan. Zaune nake a parlour ina dudduba jerin sunayen mata da matasan da nasa a É—iba, a karkashin paudasion É—ina domin basu tallafin wasu kuÉ—aÉ—en da zai jamusu jari domin dogaro da kai na tura da kuÉ—aÉ—en tallafin izuwa asusun *HAM'NAS* paudasion. a hankali na mike tsaye tare da yin mika haÉ—e da salati, wayoyina na tattara haÉ—e da sabuwar system É—ina, na haura sama, kan bedside na ajiye su kana na haye gado dan bacci nake ji, ina so nayi baccin kafin su Naseem su shigo dan suna can side É—in su Bappa. har na kwanta na tuna da akwai maganar da nake so muyi da Bappa kan wani Company na murza karfe da ake gina shi a Lagos, mikewa nayi na fita dan ina so muje ziyarar gani da ido acikin satin nan. da gudu Nasmah ta shigo tana faÉ—in "Mommy kin ga Naseem ko jai camin jiji". Naseem shima dagudun yashigo yana binta da abun yana dariya, Fatu na biye da su tana dariya da faÉ—in "Naseem kabari kar ka sa mata". da sauri nakarasa sauka kan step na rungumo Nasmah dake falfala gudu kamar zata kife kasa nace "K.......!â˜? Mommyn Twins ce 8/19/22, 10:54 - Ummi Tandama😇: "Kai Naseem me zaka sa mata kai ka bari zata faÉ—i fa kabari." nayi maganar ina É—ago Nasmah cak na rungume ta a jikina, shiko dariyar yake yana matsowa in da muke ya É—aga hannun sa sama tare da yin É—agelgel da kafa, yana washe baki, na ce "Idan ka zo nan sai na mare ka, zo kagani zo ka samata kagani, dariya sosai yarika yana faÉ—in "Mommy dan tamata ne dan ta mata wannan." "To ka samata kagani sai na maka bulala." kiran Talatu mai kula dasu nashiga yi ina faÉ—in "Talatu zo ki kaishi wa É—awisu ta cakwaÉ—e shi tun da dai shima sa mata jiji zaiyi." Talatu ta iso da sauri tana faÉ—in "Ayi hakuri Hajiya kar a kaishi wa É—awisu zata cake shi, zo nan Naseem kada kasa mata ko, so kake a kaika wa É—awisu ta cake ka,zo ko É—an lele na mene ne zaka sawa Nasmah É—in?." É—an karamin tafin hannunsa da ya dunkule ya buÉ—e kaÉ—an ya nuna mata kana ya kuma dun kulewa yana cigaba da dariya, "Lalala shine zaka sa mata?." cewar Talatu tayi maganar haÉ—e da dariya, kai ya gyaÉ—a yana washe baki, duban Fatu nayi ina faÉ—in "Wato Fatu keda Naseem kuke sawa Nasmah ta abin tsoro ko? to bazata sake wasa da ku ba." dariya Fatu tayi tare da faÉ—in "Allah Adda HAMDAH kin ga bansan in da yasamo ba kawai ganin sa nayi ya shigo da shi a hannunsa,malam buÉ—e takarda ne fa." "Au malam buÉ—e takarda ne ya É—auko shine yake so ya sa mata to bari yagani sai an kaishi wa É—awisu shima, shine baki karÉ“a ba ko Fatu kika tayashi tsoratar da ita." "Allah Adda HAMDAH binshi nake na karÉ“a shine yagudu." Talatu ta É—auke shi tabuÉ—e hannunsa taciro abun tana faÉ—in "Kawo shi nan a yasar da shi kada ka saka mata kaga tana jin tsoro, kaima kada ka sake É—auka a hannun ka." tana rike da hannunsa tafita waje ta yasar da shi kana suka dawo ciki. karaso wa cikin parlour nayi na zauna kan kujera tare da zaunar da Nasmah kan cinya ta, na dubi Fatu nace "Fatu Bappa na ciki ne?." tace "A'a yafita". sai kuma ta turo baki gaba tare da faÉ—in "Adda HAMDAH nifa wannan sunan Fatun nace ki dai na faÉ—in shi, Fatun nan fa a can Ruga ne fa ake kiran Fatun nan tun da yanzu mutum yazo birni har yanzu ayi ta ce mishi wani Fatu, gaskiya Adda HAMDAH ni wlh na canza suna Fatu ai duk su Inna wuro ne suka wani lankwasa min suna yaya Mahmoud dake shi a birni yake ai Fatima yake cemin,haka jiya wata Æ´ar ajin mu tana ta min dariya wai ni Fatu, aradun Allah na canza suna ko a ajin mu ma na faÉ—a na canza suna". dariya muka tuntsire da shi, Talatu tace "To Fatu man yan gari me kike so ace miki kenan?". "Ai sunana da yawa masu daÉ—i ma, Nana, Fatima, FaÉ—imatu, Faty Zarah duka gasunan masu daÉ—i sai a rika cewa mutum wani Fatu kamar rugo". nace "To lallai kam kamar kin sani da ma kam wannan sunan bai dace da ke ba yanzu dai kawai Faty za'a rika ce miki." tace "Yauwaaa Adda HAMDAH Faty wlh yama fi amma kuna ta cemin wani Fatu kamar rogo". "Hhhhh Faty kenan Allah bakida dama". tace "Yauwa Adda HAMDAH gashi kin iya faÉ—in sunan dai-dai mai daÉ—i". kai kawai na girgiza ina dariyar ta. tace "Zo muje muyi wasan mu o Nasmah." nace "O'o kuje bazata biku ba kuje kusata kuka bazata biku ba kam kutafi ku." "Allah bazan barshi yasa mata ba". fuskata na kawo dai-dai fuskar Nasmah nace "Zaki bisu?". kai ta gyaÉ—a "To muje daga gun na duba ko Bappa ya dawo". nafaÉ—a ina mikewa na direta kasa tare da ruko hannunta muka nufi side É—in su Inna wuro. a parlour muka tadda Inna wuro Bappa bai dawo ba sai na zauna muna É—an taÉ“a hira da ita. muna nan zaune har Bappa ya shigo yazauna muka cigaba da hirar da shi, acikin hirar nake yi masa maganar yace kwarai kuwa ya dace kam aje domin a ganewa ido, in yaso satin sama sai a je, duk da akwai idanu da yawa akan lamarin. nace "Toh Allah yakai mu." muna zaune sai ganin Naseem mukayi ya kin kimo school bag É—in Faty, a tsakiyar parlour'n ya zauna ya tuttuÉ—e littatafan cikin jakar kasa ya É—auki littafi guda ya buÉ—e yana ta gwalaÉ“e wai shi yana karatu. dariya duka muka saka, Faty ko da gudu ta mike taje ta tattari litattafan ta tana ta faÉ—in "Kai kasan meye a ciki ka iya karatu ne". Inna woro tace "To ai karatun yake baki gani ba". cikin muryar dariya nace "Um karatu yake ko gwalaÉ“e har da wani mike kafa kamar mai karatun gaskiya." "Ah to gaskiya za'a saku a makaran ta tun da har ka iya É—auko littafi kazauna ka buÉ—e kana karatu". cewar Bappa yana yi masa dariya. "Wlh Bappa nima dama ina so a turasu makaranta amma a sona sai sun cika shekara uku da rabi, amma gashi nan bakin su ya buÉ—e kawai sutafi yanzu." Bappa ya jinjina kai kana yace "Kwarai kuwa ya kama ta kam tun yanzu, tun da ga bakin su nata kan buÉ—e wa a kai su makaranta yakarasa buÉ—ewar a can".... A cikin satin akayi musu komai da komai nashiga makaranta, sai dai wata makarantar daban badaga cikin nawa ba, dan *HAM'NAS* International School Of Science Of Technology. suna da nisa saka nin mu, duk da dai shima makarantar da aka sasun yana da É—an nisa sai dai baikai su nisa ba, Islamiyar da a kasasu kuma anan unguwar tamu yake. ranar da zasu fara zuwa kuwa zo kaga murna wajen su, da misalin karfe 7 na safiya Talatu taga ma shirya su tsaf, Zulai kuma ta shirya musu lafiyayyen breakfast É—in su. ina rike da hannun su muka fito in da Talatu ke biye da mu rike da school bag É—in su da baske, parking lot muka nufa, tun kan mukaraso Yakubu direba dake goge mota yayi hanzarin buÉ—e marfin motar, cike da ladabi yaÉ—an duka yana faÉ—in "Barka da safiya Hajiya." "Yauwa barka." nafaÉ—a cikin É—an jin nauyin yan da suke yimin idan zasu gaida ni, duk kanin ma'aikatan gidan sun girme min nesa ba kusa ba wasu ma sun haife ni sun juya,nakan ji nauyi a duk san da sukayi min irin wannan gaisuwar. Nasmah naÉ—aga nasaka ta cikin motar, Naseem kam cemin yayi shi da kan sa zai shi, Talatu tayi dariya tana saka musu school bag É—in cikin mota tace "Naseem iyayen rigima kai bazaka bari a saka ka ba da kan ka zaka shi ka girma ashe". kai ya gyaÉ—a yana gyara zama tare da faÉ—in "Eh nagima da kaina naciga." tace "To babban zance ke kuma Nasmah yaushe zaki girma?". Nasmah ta cuno É—an karamin bakin ta gaba tace "Gobe dan gima ai". murmushi nayi tare da shafa gefen suskar ta nace "Au ke sai gobe zakiyi girman naki?". kai ta gyaÉ—a tana murmushi, kansu na shafa dukansu nace "To sai an dawo ayi karatu sosai kunji". sukace to. direba yaja mota ina É—aga musu hannu suma suna daga min mai gadi yawangale get suka fita.. Kwana uku kullum cikin É—oki suke zuwa makarantar ranar na huÉ—u kuwa É—oki tafara kare wa, ina kwance sai ga Nasmah ta shigo da gudu É—aure da É—an karamin towel É—in wankan su tahaye gado ta É“oye a baya na tana faÉ—in "Ni bajan je school in ba." zanyi magana sai ga Naseem shima da wandon uniform ajikin sa babu riga, sai muryar Talatu daga bakin kofa tana faÉ—in "Kai Naseem kazo nakarasa saka maka kayan". mikewa nayi zaune ina faÉ—in "A'a yaya ne tsaya mana". ai kan kace me shima ya É—ale gadon cikin cuno baki gaba Nasmah ta daÉ—a laÉ“ewa jikina tana faÉ—in "Ni Mommy bajan je School in ba". ido na waro ina duban Naseem shima da yake faÉ—in "Nima bayan jeba". kai na langwaÉ“ar gefe nace "Oh yanzu wa School É—in kuke gudu ne, bazaku je ba kuma, yaushe ne kuka fara zuwan da har zaku fara fashin sa?, kuna ji ko kuzo ku je makaranta". kafaÉ—a suka make alamar o'o, rungumo su nayi dukan su ajikina ina murmushi kana nace "Ina kallon da mukayi jiyan naaan na sojojin naaan, to waye meson zama irin su a cikin ku?". da sauri Naseem ya mike a jikina yana washe baki tare da nuna kanshi yana faÉ—in "Nine-nine". "Yau wa to har in kana son kazama soja to ko sai kaje makaranta, kaje makaranta kayi karatu sosai daga nan zaka zamo soja, in kuma baka so to kazauna kawai a gida ina baka so kazama sojan zauna abin ka kada kaje School". kai yashiga girgizawa da sauri yace "A'a a'a Mommy ina so to danje School in nine toja". "Yauwa to kada ka sake cewa bazakaje School ba dan soja baya fashin School, Nasmah ta kefa? baki son zama sojan ne?." da sauri tace "Ina to." nace "To ke bama soja zaki zama ba Dr Nasmah ce a nan, ina kina so kizamo likita kirika yiwa mutane allura." ta gyada kanta da sauri, nace "Yauwa kinga in kikaje makaranta kikayi karatu da yawa to zaki rika yiwa mutane allura". kuma gyaÉ—a min kai tayi da sauri tun kan in karasa maganar, murmushi nayi ina shafa kansu. kallon kofa nayi tare da É—aga murya nace "Talatu kawo musu uniform É—in su saka". daga can bakin kofar in da take tsaye ta waje ta amsa da to kana taturo kofar tare da sallam, nakarÉ“i uniform É—in nafara sakawa Naseem rigar sa wan da shi dama ta saka masa wandon shine yagudu,gyara masa zamar rigar nake ina faÉ—in "Um kaga soja wannan yaro zai iya rike bindiga in ya girma ya zama soja". baki yarika washewa yana É—aÉ—É—aga kafaÉ—a da faÉ—in "Nine toja ai nine toja". "Ai kam ga sojan gasken gaske". a haka nagama kimsashi kana nasakawa Nasmah ita ma inata faÉ—in mata itace Dr zata rika yiwa mutane allura. nariko hannun su muka fito parlour nan muka iske Zulai da kayan break É—in su, Talatu kuma ta É—auko musu School bag É—in su, muka nufi parking space, da murna suka shige cikin motar Naseem sai faÉ—i yake nine toja, Nasmah kuwa ta dube ni tace "Mommy ni meye?". kumatun ta naja nace "Kece Dr me yiwa mutane allura". sai washe baki suke cike da murna direba yaja motar suka tafi. Wani sati na gewayo wa muka fara shirin tafiya ziyarar gani da ido nan muka É—auki hanyar zuwa Lagos, sai dai wannan karon bantafi da su Nasmah ba saboda School, ni da Bappa da wasu jagorori biyu muka tafi, mun isa Lagos lafiya awani kayataccen hotel akayi mana masauki, mun isa yau washegari muka nufi Company da ake ta kan ginashi tamfatsetsen Company wan da girman sa ya kai ya kawo, an kai ni gurare da dama acikin sa an nunnuna min, masha Allah komai yayi saura kaÉ—an a kammala. a gajiye muka koma masaukin mu kansan cewar da kafa akayi ta yawo damu acikin Company'n. kayan jikina na tuÉ“e nashiga baya na watsa ruwa kana nafito na sauya kaya na haye gado dan na É—an huta, waya ta na É—auka na laluÉ“o lambar Talatu bugu É—aya ana biyu ta É—aga, da sallama bayan mun gaisa nace "Ina mutanen naki?". tace "Gamu nan muna tare da su a parlour muna kallo, ungo Naseem karÉ“a ga Mommy tana magana." tasaka masa wayar a kunne, "Mommy da mu biki kijo jike da mu". murmushi nayi jin muryar Naseem nace "To zan zo naje da ku, kuna karato sosai ko?". kai ya gaÉ—a, Talatu tace "Ka amsa da baki ai bata ganin ka". yace "Eh." "To a dage sosai, bawa Nasmah wayar." ya mika mata Nasmah tace "Mommy kina ina, damu biki kije da mu". nace "Nasmah to zan dawo nazo naje da ku kinji." "Mommy yaushe zaki jo?." "Gobe zan dawo naje da ku kinji". to tace, haka sukayi ta zuba min surutu da gwalaÉ“en su ni ma ina biye misu kun kai minti 30 a haka daga bisani na kashe wayar. na gyara kwanciya ta dan bacci nake ji. kwanan mu uku a Lagos muka juya Abuja. Yau asabar ba makaranta muna tare da Æ´aÆ´ana a parlour munata sharholiyar mu cikin farin ciki da jin daÉ—e, duban daular da nake ciki a rayuwa da nake yin ta yan zu nayi, Allah yabani duniya ya É—aga ni ya É—aukaka min daraja ta, a lokacin da duniyar ke kokarin suÉ“uce min a lokacin da rayuwa ta tazomo tamkar kwai a cikin tray, wan da yazamo baki-baki saura kiris ya suÉ“uce kasa ya tarwatse. numfashi na sauke lokacin da tunanin Inna ta ya zomin, wasu zafafan kwalla ne suka zubo min, Allah sarki Inna ta tabbas na yarda wani hanin ga Allah baiwa ce, ya É—auke ta a lokacin da nake tsananin bukatar ta arayuwa ta, lokacin da duniya ta juya min baya lokacin da narasa madafar dafawa lokacin da na gwammaci mutuwa ta da rayuwa ta. ya É—aukaka darajata abayan bata nan ya azirtani da arziki mai tarin yawa, wa zai iyayin duk wannan in banda *RABBUSSAMAWATI WAL'ARDI*. Allah sarki Inna ta Allah yakai haske kabarin ki ya sa mutuwa yazame miki hutu. wasu kwallan nakuma sharewa lokacin da na kuma tunawa da wata uwar wato Mama mai awara, Allah sarki rayuwa ta cito ni lokacin da duniya tafara wasan kwallo da ni, matar data jajirce wajen ganin an ceto rayuwa ta gun haihuwa, da awancan lokacin bata samo kuÉ—in da za'a min cs ba wata kila da yanzu na mutu da ni da su duka aciki, tarike ni tamkar É—iyar da ta haifa a cikin ta. lokacin da tayi nisa wajen ceto rayuwa ta sai ta tsuÉ“uce min. sai gashi yau Bappa yamaye gurbin su, yazame min uba kuma uwa, ya jajirce yatsaya kan lamari na yazamo silar isata matakin danake yanzu, matar sa ta zame min uwa Æ´aÆ´an sa suka zame min yan'uwa. Rungume su Naseem nayi a jikina ina jin wani irin kuna, rumtse idanuna nayi da karfi jin kaina yana wani irin tsara min, lokacin da tunanin abun da yayi silan rabani da ahalina yashiga yimin yawo a kwakwalwa da zuciya ta. zunbur na mike nashige bedroom É—ina, sam bana son narika tunawa da hakan duk ranar da na tuna nakan kwana cikin kunci da bakin ciki da matsanancin ciwon kai, dan ranar zan kwana ina kuka. Zubewa nayi kan kado nakife fukata jikin pillow, kai na rika juyawa ina ta fafutukar son na mance da tunanin, amma ina sai daÉ—e tahomin yake, da karfi cikin karaji narika faÉ—in "Wlh Allah Abba ban taÉ“a ai kata zina ba, Ya SALEEM ba wani É—a na mijin daya taÉ“a sani na mace bayan kai, duk da karancin shekaru na Inna ta ta tsoratar dani haÉ—e da kyamatar dani illan dake cikin zina, Ya SALEEM kai ka sanar dani mene ne aure, a lokacin da kuma nasan mene ne auren akayi min kagen zina aka kuma sheganta min Æ´aÆ´a, bazan taÉ“a aikata zina ko da ace bani da aure bare ina da shi É—in." wani irin kuka ne ya tsuÉ“uce min, na kankame jikin pillow'n ina cigaba da kuka mai tsanini. nakai tsawon awa guda ina kukan kana da kyar na sai-saita zuciya ta na baiwa kai na da kai na hakuri, kana nagyara kwanciya ta wan da ba bacci nayi ba, sai tulin tunani daban-daban. har yamma ina nan kwance, ganin tunani yana kokarin kassara ni sai na mike nanufi side É—in su Bappa, a can na iske su Naseem, har dare muna can sai wajen bayan sallar isha kafin muka koma side din mu. zuwa lokacin kam naji saukin damuwa ta kwarai dan su Inna wuro sun yaye min shi da hirarsu mai É—ebe kewa. Washegari Lahadi ma ban yarda na zauna a side É—i na ba da sassafe na wuce part É—in su Inna wuro acan mukayi breakfast, a nan nawuni muna hirar mu cikin jin daÉ—i. Yau Monday da misalin karfe 7 narako su Nasmah har sai da naga tashin su kafin na koma ciki, ina gama abun da zanyi nawuce side É—in su Bappa, ina shiga bayan mun gaisa Bappa yake cemin "Dama yanzu nake da shirin niman ki, kan ai kin masallacin nan ne harfa an rigada an gama shi, wan da aka bashi kwangilar jiya yake sanar min da cewa an gama." da murmushi sosai kan fuskata nace "Kai masha Allah kai amma dai ai kin yamin sauri wlh." Bappa yayi murmushi tare da faÉ—in "In dai da kuÉ—i a kasa komai cikin sauki yake zuwa, in dai da kuÉ—i ai komai mai sauki ne Allah dai yaba da ikon cin jarabawar da yayi dan shi kanshi arziki babban jarabawa ne, yakan kai mutum wuta yakan kaishi aljanna, kuÉ—i kamar takwabi yake idan kayi jahadi da shi shigar aljanna mai sauki ne idan ka ai kata É“arna da shi shiga wuta mai sauki ne, Allah yasa mudace." Amin Amin. duk muka amsa da shi cikin washe baki nace "Bappa masallacin nan fa nagina ne saboda Inna duk ladar arika kai mata kabarin ta, shima asibitin da yanzu ake gina shi idan a ka gama komai kyauta za'a rika yi duk ladar arika kai mata cikin kabarin ta". "Masha Allah masha Allah". abun da Bappa da Inna wuro suka rika faÉ—a kena. Bappa yace "Ubangiji Allah ya tabbatar mana da hakan Allah yajikanta da rahama ya kai mata dukkanin ladan kabarin ta ya kyautata namu bayan nasu, kai sannu HAMDAH kinyi tunani kwarai da gaske Allah ya saka miki da mafificin rahama." Amin. nace ina mai jin sanyi da daÉ—in addu'ar da yake min. Muna nan zaune a parlour ban ankara ba sai gani nayi karfe 12 har da É—ori, wayata na É—aga da sauri ina faÉ—in "Ikon Allah lallai guri babu wuya dubi 12 har ta gota an yama Yakubu yadawo kuwa bari dai na kirashi naji." nayi maganar ina laluÉ“o lambar sa, wayar tayi ta ring bai É—aga ba, nakira yakai sau biyar bai É—aga ba, na sauke wayar ina faÉ—in "Oh to ya ajiye wayar a ina ne shi ga lokacin É—auko su Nasmah daga School yayi, gashi nayi ta kiransa bai É—aga wayar ba." Bappa yace "Ko ina ya aje wayar to shi, ina yaje haka ayi ta kirashin baya É—aga wa". nace "Wlh É—azu ne na ai keshi gidan Hajiya Firdausi matar ministar Bukar, akwai wasu kayan da tayi min tallar su wan da tayi odar su daga jamani, to sun yi min na tura da kuÉ—in to É—azu take faÉ—a min direban ta baya nan ko zan turo nawa direban ya amso min, shine na tura shi to gashi har yanzu bai dawo ba nayi ta kiran shi ma bai É—auka ba". nayi maganar ina kuma É—aga wayar nakuma niman lambar sa. Hajiya Firdausi matar ministan Abuja ne, na yar da idan Allah yayi maka rufin asiri babu irin mutanen da bazaka gani ba ka kuma yi tarayya da suba, ire-iren irin waÉ—an nan matan manya muna hulÉ—a da su sosai wasu sun girme min nesa ba kusa ba, wasu ma sun haife ni sun juya amma haka muke cuÉ—an ya da su. Mikewa nayi da sauri ganin na kuma kiran sa har sau biyu nan ma bai É—aga ba, nace "Bappa bari naje kawai na É—auko su har yanzu bai É—aga wayar ba, kar suyi ta jira kasan mutumin ka yanzu haka yana kan musu rigimar zai dawo gida". Bappa yace "Maza hanzarta kam ga guri nata kan tafiya". da sauri nafita ina shiga side É—ina mayafi kawai na yafa dan dama a kimtse nake na É—au É—aya daga cikin makullen mota da suke cikin drower, da sauri na sauka na nufi parking space. kana nashiga motar nayi wa motar key, tun kafin na karaso bakin get maigadi ya wangale min get yana fadin "Adawo lafiya". Saboda yanayin gosulo na bata lokaci sosai a hanya dan har karfe É—aya ta cika har ta É—an gota, kafin nan na isa makarantar su. tun kafin nakaraso get É—in makarantar, na zubawa kofar makarantar ido sosai dan ganin wasu yara rike a hannun wani mutum "Kamar su". nafaÉ—a a file, nayi saurin isowa gurin, da mamaki nazuba musu ido ganin suÉ—en ne, yana rike da su suko sai washe baki suke, shikuma mutumin yana ta tafiya da su yana nufar wata mota dake fake taÉ—an can gefe da get É—in makarantar, yayin da yake ta girgiza kai alamun yana jin surutun da suke ta zuba masa. cikin hanzari na isa gefe nafaka cike da mamakin ganin nufar motar yake gadan-gadan na É“alle marfin mota na fita da sauri, cikin hanzari nasoma bin bayansu ina faÉ—in "Kai Naseem Nasmah!, malam ina zaka kaisu kuzo nan ku wuce mutafi". mutumin bai juya ba sai su yaran ne suka juyo sai kuma suka kawar da kansu suka juya suka cigaba da tafiya suna cigaba da zuba masa surutu. da sauri nasha gaban su gani yan da suka batsar kamar basu sanni ba nace "Kai ina muku magana kuna jina ina zakuje kuwuce mutafi malam ina zaka kaisu?". sai sannan mutumin yaÉ—an dukar da kansa dai-dai tsawon su kana yasoma magana "Kunsan ta ne?." batare da yaÉ—ago ko ya dube ni ba ya ce "Ke a ina kika sannu bamu hanya mu wuce." ido na waro cike da mamaki jin abun da yafaÉ—a tare da mamaita kalmar nasa "Nasan su? nasan su fa kace, da alla malam ka sake su ina magana kana cigaba da tafiya da su." gefe na ya gota batare da yace komai ba ya karasa jikin motar nima da sauri na rufa musu baya ina cigaba da faÉ—in "Kai malam ina tambayar ka ina zaka kai su wai kana tambaya ta nasan su ne, ni zaka tambaye ni nasan sune, tambaya ta kake nasan su? dalla kasake min yara muwuce,ina ne zaka dasu kake nufar cikin mota da su?, idan baka sake suba yanzu-yanzu zan kira maka hukuma anan." baiyi magana ba sai mika hannun sa yayi yabuÉ—e marfin motar, yaÉ—au ko kwalin chocolate yaciro chocolate guda huÉ—u yabawa Nasmah biyu ya baiwa Naseem biyu kana yace "To ga tsarabar ku kuci wannan yanzu, wannan kuma sai kusa a aljuhu." yafaÉ—a yana cusa musu wani chocolate É—in cikin aljuhun wandon su. da mamaki nake kallon su ganin yan da sukayi tamkar basu sanni ba, sai murna da tsalle suke suna faÉ—in "Ye am bamu da yawa ye am bamu da yawa." cikin takaici nakai hannu zan fisge chocolate É—in, da sauri mutumin ya janye su gefe kana yaÉ—ago kansa tare da zuba idanun sa cikin nawa, wani irin dirrr naji a cikin jikina tamkar jan wutan lantar ki.......! Mommyn Twins ce 8/19/22, 10:54 - Ummi Tandama😇: Mai gadi yashiga jan hanci yanaci gaba da faÉ—in "Sam babu wan yafita ai da nasani dana shiga ciki naje na karÉ“i makullin mota naje na É—auko su ai, na É—an iya mota ba sosai ba amma da wasu su É—auke su gara ni naje a haka na É—auko sun, wasu matsiya tane masu niman jaraba suka É—auke su, duk tai makon da akewa mutane baiyi musuba har sai sun haÉ—a da sata, wayyo Allah Naseem wayyo Nasmah, ashe da rabon ragowar shayi da nama gobe bazan shaba, kullum sai sun kawo min na haÉ—a da nawa duk na kallame." zuwa yanzu tashin hankalin Bappa yafara bayyana yashiga faÉ—in "Kanu innalillahiwa'inna'ilaihirraji'un Allahumma ahjirni fi musibati²." bakina na toshe da tafin hannuna jin kuka mai sauti yana son suÉ“uce min najuya ina kokarin barin gurin Bappa yakira sunana najuyo ina hawaye yace "Je ki zauna kada ki É—aga hankali sosai na tabbata zasu kira kuma bazasu cutar da su ba dan kuÉ—i suke bukata za'a kuma basu babu komai." kai kawai na gwaÉ—a najuya nasoma tafiya, maigadi yabiyo ni yana cigaba da jan hanci yace "Anyi bako Hajiya." ban iya juyowa ba bare nabashi amsa Bappa ne yace "Ina bakon?." yace "Gashi can a mota yana shigowa kuma kuka shigo," "Wanene?." cewar Bappa, yace "Gashi can cikin mota ai da naso hanashi shiga ganin baiyi kama da irin waÉ—an da za'a dakatar ba shine na barshi ya shigo." yayi maganar yana nuna wata mota dake fake gefe a farfajiyar gidan. Bappa ya girgiza kai kana ya soma tafiya yana faÉ—in. "Ana cikin wani hali ta ya za'ayi a saurari wani bako." Cikin matukar da muwa da tashin hankali nake tafiya, "Me zaisa su É—auke su in dai kuÉ—i ne akan su É—auke su ni da sun faÉ—a min ko nawa ne zan basu, me yasa suka zaÉ“i su cutar da yaran da basujiba basu gani ba. wlh Allah sai yabi musu kadin su tun suna ciki ake cutar dasu da zaluntar su, har suka fito duniya." wasu zafafan kwalla ne suka rika wanke min fuska bana ko iya ganin gabana, tunani na É—aya awani hali suke yanzu.. Bappa har ya wuce motar da mai gadi yace masa bako ne ciki, sai kuma ya dawo sanin da yayi kan cewa bako rahama ne, gilashin motar ya kwankwasa, a hankali aka zuge glass É—in. cikin matukar mamaki Bappa ke lallon mutumin da waÉ—an da ke tare da shi, yana zaune a mazaunin direba waya na rike a hannunsa yana ta faman latsawa, Nasmah na zaune a gefen sa tasaka kanta jikin kafaÉ—ar sa tana ta cin chocolate, Naseem kuwa na zaune a gefen mai zaman banza rike da waya a hannunsa yana buga game yana kuma taunar chocolate. cikin tsananin matukar mamaki Bappa ke cigaba da kallon mutumin da mamakin ganin sa tare da su Naseem, tabbas bazai taÉ“a mance wannan fuskar ba, mutumin daya samar musu da ingantaccen ilimi a rugar su,mutumin da ya yayi ruwa yayi tsaki wajen ganin an cafke Æ´an ta'addan da suke shiga rugar su suna kaÉ—a musu shanukai su kashe musu makiyaya. cikin girmamawa mutumin yashiga gai da Bappa, Bappa ya amsa fuska É—auke da annuri yana yi masa kallon sani, shiko mutumin ga duk kan alamu bai gane shiba, cike da al'ajabin ganin su tare da su Nasmah Bappa yace, "Ikon Allah kai ne nan tare da su Naseem da muke zaton ko Æ´an garkuwa da mutane ne suka É—auke su." da sauri Bappa ya juya yana faÉ—in "HAMDAH taho gasu nan." cak naja na tsaya dai-dai lokacin dana ke kokarin É—aura hannuna jikin kofar side É—ina, najuyo da sauri, magana Bappa yaci gaba dayi yana nuna cikin motar. "Gasu nan cikin mota Allah yayi ikon sa." dagudu na nufo gun motar ina share hawaye na da bakin mayafi na, ina isa gun motar nawuce gaban Bappa da sauri batare da duban cikin motar ba duk da glass É—in motar a sauke take, hankali na nakan murfin motar dana saka hannu ina kokarin buÉ—e motar sai jin ta nayi a rufe, da sauri na É—ago karaf idanun mu ya haÉ—u da juna, da mamaki nake kallon sa sai kuma nan take naji raina ya É“aci, mutumin da yace wai arika turo mai wayo yarika É—aukar su Naseem a school ba ni ba, wan da kuma suke kiran sa da Daddy yayi ta tara musu chocolate kamar sun zama shazumame sar kin shan zaki. fuska na É—aure tamau ina duban su Nasmah nace "Ku sauko nan!." nayi maganar cikin tsawa da zare idanuna. Bappa yaÉ—an matso yana faÉ—in "Wlh mun shiga tashin hankali sosai da akace wani mota daban yazo ya É—auke su ba É—aya daga cikin motocin gidan nan ba, mungama zaton masu garkuwa da mutane ne, suka É—au ke su." kai ya jinjina tare da yin murmushi wan da yayi sana diyyar bayyanar kyakkyawar dimple É—in fuskar sa, batare da yayi magana ba ya kai hannu ya buÉ—e marfin motar, baya na É—an ja kaÉ—an ya buÉ—o marfin, ya zuro kafafun sa waje, Nasmah dake gefen sa yaÉ—ago ta cak yafito da ita ya aje ta kasa, kana asannu yafito daga cikin motar,tsayuwar sa ya gyara kana yaÉ—an sunkuya jikin kofar yamika hannu cikin motar Naseem ya rike hannun nasa yaÉ—ago shi cak yafito da shi, sai da ya ajiye Naseem kasa kana ya É—ago da murmushi yace. "Idan za'a cigaba da barin su har kowa ya watse a makaranta ba'a je ana É—aukar su kan lokaci ba to kuwa zasu iya fuskantar hakan,domin su masu garkuwa da mutanen babu ta in da basa nan." kai Bappa ya jinjina cike da gamsuwa da maganar sa kana yace "Tabbas kuwa, Allah yashiga sakanin nagari da mugu." a kufule nace "Babu ranar da ba'a zuwa É—aukar su kan lokaci in ban da ranar da nayi ta kiran Yakubu bai É—aga ba, sai kuma yau, yau É—in ma ai bawani makara akayi ba tun da karfe 12:50pm muka isa makarantar kuma karfi 12 da rabi ake tashin su, kuma tun kan É—alibai su watse mai gadi yace aka É—auke su, to ashe dai ba'a makara zuwa É—aukar su, ana zuwa É—aukar su tun shabiyu ajira su har sai an tashe su a É—auko su a dawo da su, babu wani É“ata lokaci a zuwa É—aukar su, kai kuwuce mushiga ciki!." nayi maganar cikin haÉ—a haushi biyu zuwa uku, akan me zaice ba'a zuwa É—aukar su kan lokaci. sannan kuma wace dalilin ne yasashi zuwa É—aukarsu ina ruwan shi dasu dakuma rayuwar su, yasa nayi kuka da tunanin ansace su ne. sannan ganin yan da yaran suka manne masa sai kiran sa da sunan dana hanasu suke. tun da nafara maganar idanunsa akaina yayin da yake shafa sajen fuskar sa, kafaÉ—a yaÉ—aga kana yace "Kinyi kokari, kiyi wayon sanin hakan tukun dan da kaÉ—an kikafi yaran wayo." ido na waro amma lallai mutumin nan yana da rainin wayo karo na biyu kenan da yake cemin wai bani da wayo, yaran dana haifa yake cewa wai dakaÉ—an nafisu wayo. wani kallo na watsa masa tare da murguÉ—a baki nace "Allah yasa wayon suka fini, mece ce matsalar ka?." nayi maganar tare da kuma murguÉ—e baki. Bappa yace "Um to hakane kam amma ana zuwa É—aukar su akan lokaci sai dai É“acin rana, amma akiyayen shiyafi, mun gode sosai, in sha Allahu za'a kara azama wajen zuwa É—aukar su." hannunsu na fizgo ina faÉ—in "Kuzo ku wuce ina magana kuna tsaye." najanyo su fuuu muka nufi ciki anan na barsu shi da Bappa, cikin haushin jin Bappa yana saurarar sa, har shi zai gwada wa mutane yan da zasuyi da rayuwar su, ina ruwanshi, irin mutane masu shegen shishshigi kan abun da bai shafe su ba. sai da muka shiga parlour kafin na sake hannun su, na zauna kan kujera, ina duban su sukam ma ko a jikin su sai wata tsafgar su suke. kunnuwan ko wannen su na rike naÉ—an murÉ—a da karfi, suka haÉ—a baki wajen cewa "Wayyo Mommy." nace "Sai na sinke kunnen har idan baku dai na abun da na hana kuba, wato duk hanaku da nake tayi bakuji ba ko shine yau abun naku yagirma har da binsa, kunsan shi ne? baku san mutum ba kukama binsa har da shiga motar sa, ina kuna so a yanka kanku ne?." kai suka girgiza da sauri tare da faÉ—in "A'a-a'a Mommy." nace "To ban hanaku ce masa Daddy ba bana ce muku ku bakuda Daddy nice Mommyn ku nice Daddyn ku ba?, ban ce kada wani ya sake baku abu ku karÉ“a kuci ba?, shine har yau zaku bishi kushiga motar sa, kunsan shine?, to sai nayi muku duka yau sai na kaiku wa É—awisu ta caccake ku bari ku gani." namike tsaye tare da ruko hannun su ina cigaba da faÉ—in "ÆŠawisu kawai zan kai ku wasu sune zasu yin maganin ku." kuka suka sake da karfi suna faÉ—in "Wayyo Mommy kai ki kai mu." "Ai bazaku bari ba sai na kai ku gurin su su hana ku da kansu." nayi maganar ina jansu. ihu sosai suke suna faÉ—in "Mommy mun bayi." komawa nayi na zauna kan kujera ganin sun tsorata sosai najasu jikina na rungume su, ina faÉ—in "To kuyi shiru nafasa kai ku amma idan kuka kara sai na kaiku, zaku kara ko?". kai suka girgiza da sauri nace "Kada ku sake zuwa gurin wan da baku sanshi ba bare har kushigs motar sa, kuma kada ku sake ce masa Daddy shi ba Daddyn ku bane nice nan Daddyn ku kunje jo?." kai suka kuma gyaÉ—a wa suna jan shashsheka. a hankali narika shafa kansu cikin tsananin tausayin su, wasu zazzafan kwalla ne suka ciko ido na, ban dakatar da su ba har sai da suka gangaro kan fuskata ta, nakai tafin hannuna na goge, yayin da nake daÉ—a mannna kan su a kirjina, ina jin tausayin su na daÉ—a shiga na. maganar zuci nafara yi yayin da zazzafar hawaye mai cike da É—in bin kuna ke cigaba da zuba a ido na. "Kuyi hakuri bana so ku sanya wa ranku abun da babu shi a rayuwar ku, nafiso ku tashi da sanin cewa bakuda shi ni zan zame muku garkuwa uwa uba." daÉ—a rungume su nayi ina jin kuna cikin raina lallai tabbas ba shakka anyi min tabo mai muni ni da Æ´aÆ´ana wan da bazan taÉ“a mancewa da shi a rayuwa ta ba. kwallar idanuna na share tare da kokarin danne damuwa ta. É—ago wa nayi jin sallamar Bappa na amsa ina mai cigaba da kokarin danne damuwar dake azalzala ta cikin zuciya, naÉ—an gyara zamata cikin dabara na share ragowar hawayen idona, ya karaso ya zauna. huf su Nasmah suka mike a jikina Naseem daya dubi Bappa yace "Bappa Daddy fa yana waje?." sai kuma ya juya da sauri yana faÉ—in "Dan je guyin Daddy." ido na ware da mamaki kamar ba yanzu nagama masa barazana har da kukan sa ba amma gashi ya tashi yana faÉ—in zai je gurin mutumin. Bappa yayi murmushi da faÉ—in "Dawo nan mutumina, ai yatafi." yafaÉ—a yana ruko hannunsa kana ya cigaba da faÉ—in "Yaro kenan shi kamar dabba yake duk mai kyautata masa to zakaga yana son kasan tuwa da shi, wlh nayi mamakin ganin Ahmad Tijjani Sabil, nakuma yi mamakin ganin sa tare da yaran nan, koda yake hakan ba abun mamaki bane." da É—an mamaki na dubi Bappa jin sunan mutumin a bakin sa, Bappa ko daÉ—a faÉ—aÉ—a murnushin dake bayyane kan fuskar sa yayi kana yaci gaba da faÉ—in "Yaron kirki ne sosai kinga ma bai ganeni ba sai da nayi masa tuni, ai wannan yaro Allah dai ya masa albarka yakawo babban gudunmawa cikin rayuwar mu a Ruga, ya inganta mana rayuwa yakawo haske cikin rayuwar mu kwarai da gaske, lokacin da É“arayin shanu suka addabe mu babu dare babu rana, sukashe mana makiyaya su kaÉ—a mana shanukai, kwasam sai Allah yajefo mana shi, wata rana yazo rugar mu a matsayin bako watan sa guda tare da mu, ranar da yazo É“arayin shanu suka shigo rugar mu, suka saci shanukai suka raunata mana makiyaya Allah yatakai ta kwanan su na gaba, sai dai mun rasa makiyayin mu guda É—aya kuma mun san su suka sace shi, ya kwashe su yakai su asibiti cikin gari, ranar hankali yatashi muka É—au aniyar É—aukar mataki da kanmu. ranar da ya cika sati uku, har lokacin É“arayi basu kara kawo mana hari rugar muba sai dai rugar da muke makota da su, da yammacin ranar an je kai masa abinci kamar yadda aka saba sai aka iske shi da wani makiyayin mu cikin É—akin da aka bashi yake kwana ciki, makiyayin da muke tunanin É“arayin shanun nan sun tafi da shi, ya É—aÉ—É—aure shi, yanata gana masa azaba da wani irin na'ura. wan da yakai abincin yakurma ihu nan da nan jama'a suka taru munyi mamakin ganin makiyayin mu tare da shi yana bashi azaba,nan Æ´an gari suka rika cewa a kashe shi ashe shima É“arawon shanu ne muke tare da shi. cikin tsawa yace duk mudakata yace kunzo nan kuna ta wani har gowar ku mara amfani kuje ku tare Æ´an ta addan da suka dunfaro rugar ku domin kona ku su kuma tafi da dukiyar ku. cikin rashin fahimtar abun da yake nufi muka shiga kallon junar mu, shiko ci gaba da baiwa makiyayin mu azaba yacigaba da yi, dai-dai lokacin kuwa muka soma jin karar bindiga daga can nesa, nan fa hankali yatashi jama'a suka fara kokarin watsewa domin É—aukar makamin kare kansu. wani irin gigitaccen kara makiyayin nan ya saka lokacin da ya datse masa yasar hannun sa guda, cikin tsawa yace masa, Ta wani kusurwa zasu shigo,? su nawa ne kuma?, wasu irin bindigogi ne a hannunsu?!!. cikin tsananin jin azaba yasoma magana cikin matukar wahala yashiga bashi amsar tambayar dayayi masa. munyi matukar mamakin jin abun da makiyayin nan yafaÉ—a to me haka yake nufi?, a lokacin bamu sami damar jin amsar tambayar muba, sai muryar AHMAD Tijjani Sabil mukajiyo da karfi yana faÉ—in. Kowa ya koma gidan sa kada wani yafito waje,duk abun da zakuji kada ku fito. kamar yadda yafaÉ—a kuwa haka mukayi batare da musu koni man jin ba'a si ba kowa yayi gidan sa, sai dai bamu zauna haka ba kowa da makami a hannusa domin kare kai. ranar tashin hankalin da muka shiga ba zai faÉ—u ba, dan muna shiga gida Æ´an tadaddan nan suka karaso cikin rugar mu, wasu suna kunce dabbobi wasu kuma suna ta harbi. shigowar su dakamar minti ashirin, muka jiyo jiniyar sojoji ta ko ta ina suka sanya rugar mu a tsakiya. nan suka shiga bata kashi ranar kamar rugar mu zata fashi dan harbin bindiga, an É—auki tsawon mintina 30, kafin kikaji guri yayi tsit. sai hayani ya da magana da turanci haÉ—e da hausa ake, can aka fara magana da abun sauti irin wan da hukuma suke magana da shi domin sanar wa ko bada umurni wa al'umma, aka ce kowa ya fito, nan muka fito cikin É—ar-É—ar duk da asanar wan nasu sun sanar mana da cewa hukuma ne ke magana, amma a tsorace muke kuma bamu fito haka kawai ba sai da makaman mu, domin kare kai, duk da kuwa munsan su bindiga ne a hannusu mukuma akasin haka sai dai munsan Allah yana tare da mu. koda muka fito ganin hukumar ne da gaske nan hankali yaÉ—an kwanta kaÉ—an, Allah yabasu nasarar cafke Æ´an tadaddan nan wasu daga cikin su sojojin sun harbe su gasu kwance cikin jini, wasu kuma gasunan kwance a É—aÉ—É—aure bindigogin su a zube a gefe. Ahmad Tijjani Sabil yana tsakiyar hukuman nan yayin da wannan makiyayin namu ke kwance a gabansa shima a É—aÉ—É—aure. bayan jawabi da ban hakuri da hukumar nan sukayi mana, da alkawarin bamu kariya da tsaro, suka tattari Æ´an ta'addan suka saka su cikin mota, Ahmad ya É—aga wannan makiyayin namu yatura shi cikin mota, nan wasu daga cikin sojojin suka tafi da Æ´an ta'addan suka bar motan soja guda. ranar acikin rugar mu suka kwana suna bamu tsaro kwanan su uku kafin suka tafi, Ahmad kuwa bai bar rugar ba har sai da yagina mana makaranta da asibiti yazuba mana malaman asibiti dana makaranta, makarantar ne ma Fatu take ciki, tun daga lokacin muke samin tsaro sosai, munyi matukar farin ciki da zuwan Ahmad cikin mu dan kuwa ya tallafawa rayuwar mu kwarai da gaske, har rana mai kamar ta yau ba'a kuma shiga rugar mu da sunan sata ba." Numfashi na sauke cike da alhinin labarin da Bappa ke bani nace "Ikon Allah to shi wannan makiyayin naku yaya iyayen sa sukayi dajin shima É—an fashin ne, yanzu ku duk zaman ku da shi bakusan shi ma É—an fashi bane?". yace "Sam bamusan É—an fashi bane, to ai shi asalinsa ma ba bafulatani bane, zuwa yayi rugarmu tun yana yaro yace zai rika yi mana kiwo muna biyan sa, shekaru 16 muna tare da shi, muka bashi duk wani yar da ashe macuci ne bamu sani ba, yana ha'intar mu, har sai da Allah ya turo mana Ahmad Tijjani Sabil." kai na jinjina cike da mamaki ina faÉ—in "Tab lallai to shi ya akayi yasan É—an fashi ne shi da yazo bai jima ba, ku da kukayi shekara da shekaru da shi baku sani ba?." Bappa yace "Wlh duk kanin mu kowa abun da yayi ta faÉ—a kenan bayan komai ya lafa, sai dai bamu sami amsar tambayar ba, dan ko shi Ahmad É—in da muka tambaye shi bamu sami wani kwakkwaran amsa ba, sai muma muka bar shi bamu tsanan ta masa tambayar ba, munji daÉ—i da farin cikin da Allah ya nufa shi zai zame mana karshen matsalar mu." Bappa yana maganar ne cikin nuna tsantsar farin ciki da jin daÉ—i... na ce "Lallai kam to Allah ya tsare na gaba." ya am sa da amin amin kana yamike yana faÉ—in "Bari na shiga ciki." yana tafiya naruko hannun su muka haura sama... Yauma kamar kullum narako su Naseem ina tsaye har sai da naga fitar su, kana na koma ciki, wanka nayi ina gama kimsawa nayi breakfast, wan da nasa Zulai takawo min shi cikin É—aki, ina gama breakfast É—in nahaye gado dan bacci ne a idanuna ban farka ba, sai wajen karfe shabiyu saura Æ´an mintina dabasu fi 20 ba, wayata na janyo na kira Number Yakubu, kasan cewar yau juma'a da wuri ake tashin su, bugu É—aya ana biyu ya É—aga, nace "Kayi maza kaje ka É—auko su Nasmah." yace "To Hajiya da ma nima yanzu ina kan goge motar kenan yanzu zan tafi." "Kabar wani goge mota katafi kaje ka É—auko su." nayi maganar tare da kashe wayar, mikewa nayi nashige bathroom nayi wanka tare da dauro al'wala, ina fita na sauya kaya. ganin lokacin salla da saura sai na nufi kofa nafita kasa na sauka. Talatu da Zulai duk suna parlour'n suna ganina sukayi min sannu da fitowa,na amsa ina yi musu yaya aiki, suka ce alhmdllh, an tsaftace gurin ko ina yayi tsaf sai kamshe ke tashi. ina jin matukar daÉ—in zama da su sabo da suna baiwa aikin su kulawa sosai. a É—aya daga cikin kujerun parlour'n na zauna, tare da saka idanuna kan TV ganin shirin da ake. zamata baifi da minti 10 ba najiyo muryar su Naseem daga kofa ta waje suna kwaÉ—a sallama, kallon kofar nayi da murmushi akan fuska ta, suka turo kofar da gudu suka shigo suna faÉ—in "Mommy mun dawo Mommy mun dawo." faÉ—aÉ—a murmushi na nayi tare da faÉ—in "To sannun ku da dawowa." in da nake suka taho da gudu na buÉ—e hannuna suka faÉ—o ciki na rungume su, ina dariya da faÉ—in "An yi karatu sosai dai ko?." kai Naseem ya gyaÉ—a. nace "To madallah." na dubi Nasmah nace "Likita na anyi karatu sosai ko?." itama kai ta gyaÉ—a tana washe baki, Naseem ko baki ya turo yace "Mommy ni baki ce min tojan ki ba." cikin muryar dariya nace "Oh soja na." shima dariyar yayi cike da jin daÉ—in sunan dana kira sa da shi. Nasmah ko mikewa tayi a jikina tarike kugu tare da jujjuya idanun ta tace "Ai nafi Naseem yin kayatu da yawa yana ta wasa da wani yayo, ni nayi kayatu da yawa dan yika yima mutane ayyuya kuma." ido na waro yan da take yi da ido ya bani dariya nace "A.a.a Naseem É—in wato wasa kaje ka zauna kake yi ba karatu ba ko?". nayi maganar tare da rike haÉ“a ina kallon sa, yace "Hum kaiya ne take yi, nayi kayatu da yawa kuma Daddy yace nayi kayatu da yawa idan nayi da yawa da yawa, yace dai jo ya auke mu a gida." Nasmah tace "Um ai Daddy yace ni ne dai jo ya auke ni nafika kayatu da yawa, ai nayi mishi kayatu da yawa ma yau kuma." Naseem yayi kamar zai ture ta yana faÉ—in "Ai nima nayi ma Daddy kayatu da yawa." ido na waro da mamakin kin sunan da suke ambata sunan da nayi ta musu barazana kan kuma faÉ—ar sa, nace "Kai kurafa min baki, wani Daddy'n." nayi maganar cikin tsawa dan ni a tunani na ma wani ne daban ba wancan mutumin da na kwaÉ“e su da shi ba. Yakubu da yashigo rike da school bag É—in su yakaraso ciki Talatu ta amshi jakar tayi cikin bedroom É—in su da shi, ya washe baki da faÉ—in "Ai Hajiya Ahmad Tijjani Sabil suke nufi, ai ina isa na iske su tare da shi abakin get din makarantar su tare da shi, naji yana tambayar su karatu suna ta zuba masa karatun da aka musu, nace kai ashe fa yaran nan za'ayi masu ilimi ne anan wlh kuwa." yayi maganar yana mai cigaba da washe baki. fuska na tsuke sosai tare da mai da dubana kan yaran kana na mike tsaye na ruko hannun su na janyo su muka haura sama, muna shiga É—aki na sake su ina faÉ—in "Ni Æ´asu yazan yi da yaran nan wato ku bakwa ji, duk abun da zanyi ta faÉ—a muku bazaku jiba shi wannan Ahmad yake ko wane wlh dole na É—au mataki a kansa, idan bana É—au mataki akan lamarin ba zai rushe min ginin danake ta gina shi, yana ta kokarin rushewa ya haka ne kam, ina ruwan shi da su meye haÉ—in shi da su da zai rika sanya musu wani ra'ayi a cikin zukatan su." Duban yaran nayi nama rasa wani irin masifa zan musu, ko da na musu ma abanza gobe zasu kuma, zubewa nayi bakin gado da tunanin yan da zanyi na É“ullo wa lamarin, yazama dole na É—auki mataki kan lamarin idan ba hakaba, to kuwa tabbas ginin da nake ta kokarin gina shi domin yayi karko to kuwa zai iya rusa min shi, tabbas zan É—auki mataki kansa, "Amma mene ne mafita?. nayi wa kai na tambayar ina gyara zama ta, "Mafitar kenan kawai ki canza musu makaranta." zuciya ta ta bani amsa, kai na jinjina da gaskata abun da zuciya ta ta faÉ—a min, hakanne kawai mafita ta yadda zasuyi nesa da shi, idan kuma ba haka ba to kuwa abun da nake ta kokarin cire masu kwaÉ—ai tar sa a zukatan su shine zai faru, dan kuwa in har hakan yaci gaba da faruwa zasu tashi da sanin wani mahaifi a ransu wan da bana son su san haka, nice nan uwa kuma uba a rayuwar su, sam bana son su tashi da jin cewa zasu sa mi uba ni zasu cigaba da jina uwa kuma uba a rayuwar su. bana so su sanyawa ransu abun da baza su samu ba a rayuwar su, to mene ne amfanin sanya wa ransu hakan, gara kawai su san cewa ba su da uba, su ji a ransu ni ce uban nasu kuma ni ce uwan su. wannan kaÉ—ai shine mafita in sauya musu makaranta in nesan tar da su daga gare shi, in ma koyarwa yake a makarantar imma mene ne baya sake ganin su bare ya cigaba da cusa musu wani ra'ayin, ai dai sun rabu bashi basu, bazai sake ganin suba suma haka bare su sake kiran shi da wani Daddy, "ÆŠan rainin wayo har da cewa surika ce masa wani Daddy, sai kace wani uban su ko meye gamin sa da su oho." naja dogon tsaki tare da yin kwafa kana na mike, nashiga tuÉ“e musu uniform É—in su, ina faÉ—in "Ku da shi É—in duk zanyi maganin ku." bathroom na jasu da kai na nayi musu wanka yau, muka fito na saka musu wasu daga cikin kayan su da yake bedroom É—ina, sai da na nagabatar da sallar azahar kana na janyo su muka sauka kasa. dinning area muka zarce bayan munci abinci najasu muka tafi part É—in su Inna wuro, nan muka tarar da Faty ita ma dawowar ta daga school kenan, nan muka yada zango mukata hira... da yammacin ranar zaune nake a parlour'n sama na É—ago wayata na laluÉ“o number shugaban makarantar su Naseem.....! Mommyn Twins ce 8/19/22, 10:54 - Ummi Tandama😇: Yan da idanun sa yasarkafu cikin nawa haka babu zato ko sammani shi yasani shiga yanayin, sai kuma na gyara tsayuwa ta da kyau, wani kallo yake bina da shi daga sama har kasa kana yace "Na É—auka kafin kiran hukuma ihu zaki yi ta yi kitara jama'a kice ga É“arawo yazo satar yara, ke ba'a yi miki ihu ba har ke zaki wa wani ihu? karfe nawa ne yanzu wai wannan lokacin ne lokacin zuwa É—aukar yara a makaranta,abar yara can kowa ya watse sai su kaÉ—ai a cikin makaranta, sabo da baki san abun da kike yi ba an turaki É—aukar su kin tsaya kin É“ata lokaci a hanya kina damuwar ki wata kila ma kinbi gidan kawayen ki kin gama sharholiyar ki, kafin nan kika zo wai ke a hakan kinzo É—aukar su a makaranta, karfe nawa yanzu?. karfe nawa ne yanzu?!". yakuma nanata tambayar, yana maganar ne ida nunsa a kaina da kuma alamun jaddada tambayon da yake jefa min, gashi dai maganar cikin faÉ—a yake yin sa amma lamÉ“ansa a hankali suke motsawa. dogone yana da faffaÉ—ar kirji da zubin kakkarfan maza, fuskarsa na É—auke da É—an siririn saje wan da ya zagaye fuskar nasa har zuwa É—an gemun sa da bai wuce rabin kamu ba, irin gemun da gayu suke bare. baza a kirasa da fari soll ba sanna kuma ba baki bane, hasken sa dai-dai. kwantaccen gashin kansa baki sitif yasha gyara mai tsamtsi da tsulÉ“i sai wani yal-yal yake, sabo da iskar dake kaÉ—awa. Kaina nakawar gefe tare da murguÉ—a baki nashi a wanne zai zauna yana wani masifa to ina ruwan shi ne ma. É—an rutsunawa yayi yarage tsawon sa dai-dai tsawon yaran kana ya dubi ko wannen su yace "Idan kunje gida kuce wa Mommyn ku kada a sake turo Aunty ku ta É—auko a School a rika ai ko me wayo yarika É—auko ku, wan da bazai barku kuyi ta shan wahala a nan ba, kunji ko?." kai suka gyaÉ—a suna ta faman shan chocolate "Yauwa to kuje gida sai gobe zan kawo muku wani chocolate É—in, kada ku man ta in kunje gida kufaÉ—a wa Mommy kada a kuma turo wannan Aunty'n naku É—aukar ku a School a aiko mai wayo." yayi maganar yana yi musu alama da suje in da nake yana binsu da murmushi, ido na waro cikin masifa nabuÉ—i baki zanyi magana, dai-dai lokacin mota ta faka gefen mu, da mugun gudu, Yakubu direba yafito da sauri ya iso in da muka yana faÉ—in "Ranki shi daÉ—e Hajiya wlh gosulo ne yatsare ni tun É—azu babu ta yan da zanbi na koma da baya na canza wata hanyar, gaba da baya motoci suka sani a tsakiya,jibi kumatu na har mari nasha dana nimi in juya dan na canza hanya, Hajiya a gafarce ni, wlh gosulo ne, ita kuma wayar sam na mance jiya da zankwanta bacci nacire ta a kara yau har gari yawaye kuma ban mai da kararta ba, Hajiya ayi hakuri da Allah." maganar yake tamkar zai zuba guiwowin sa a kasa yana tafa bayan hannun sa a cikin É—aya tafin hannunsa alamun roko, banyi magana sai juya wa nayi nanufi gun motar dana zo da ita, dan wannan mutumin yakure É“ata min rai. Muryar Yakubu naji yana faÉ—in "A'a ranka shidaÉ—e ina wuni barka da warhaka." bude motar nayi nashige ciki batare da naji amsa gaisuwar da yake yi masa ba. sai juyawar sa nagani yamatsa jikin motar sa yana kokarin bude marfin gidan baya, da sauri a ka buÉ—e gidan gaba wani ya fito cikin hanzari yarigasa kai hannu jikin kofar yabuÉ—e, kana yaÉ—an ja dabaya ya bashi hanya yashige motar ya mai da murfin ya rufe, kana shi kuma yakoma mazaunin direba yaja motar sukayi gaba. Yakubu yakamo hannun su Naseem ya kawo su motar da nake yabuÉ—e gidan baya yasaka su, yace "Hajiya bari na rufe wancan motar sai na kaiku gida a wannan na hau abun hawa na dawo na É—auki wanca É—in." yajuya da sauri ya nufi in da motar da yazo da ita yake, fita nayi nakoma baya in da su Nasmah suke, yana kulle motar yadawo yashiga mazaunin direba yaja motar. Munbar harabar makarantar da É—an nisa kana na juyo na dubi su Nasmah dasuka gama kwaÉ“e jikin su da chocolate, ganin ina kallon su sai Nasmah ta miko min na hannuta tace "Mommy akici". cikin masifa nace "Ai sai kun sha duka ba kun iya kwaÉ—ayi ba bakusan mutum ba kuka ma binsa, waya sani ma ko mai satar mutane ne yayi gaba da ku wata kila ma badun na iso da wuri ba da yanzu yayi gaba da ku, yaje yayi kuÉ—i da kanku, idan kuka kara ganin mutum baku sanshi ba kuka bishi sai na zane ku, bare har ya baku abu ku karÉ“a sai na yanke hannun ku, yajaku mota zaiyi gaba da ku Allah ya so ku ai da kuna can Allah kaÉ—ai yasan halin da kuke ciki, badun na iso da wuri ba, É—an rainin hankali wai arika ai ko mai wayo yarika É—aukar ku to ina ruwan sa ma daku tukun, mttsss." nayi maganar tare da jan tsaki. baki Naseem yawashe cikin É—an sallen murna daga zaunen da yake yace "Ai Daddy yace dai caya mana mota." wani irin faÉ—uwar gaba naji da ya ambaci sunan Daddy da sauri nace "Kai Naseem waye kuma Daddy?." Nasmah ce ta caÉ“e zancen da faÉ—in "Daddy daya bamu chocolate yace dai cayamin jigi haida mota da chocolate da yawa." da karfi jin yan da zuciyata ke tafarfasa kai na ke sara min nace "Kai ya isa! idan na kara jin kalmar wani Daddy a bakin ku sai na fasashi, ku bani chocolate É—in nan." nafaÉ—a ina karÉ“e chocolate É—in hannun su na zuge glaas É—in motar nayi wurgi dashi. maganar Yakubu najiyo wan da tashin hankalin da nashiga ciki yanzu sama-sama nake jiyo shi yana faÉ—i "Hajiya ai shi wannan mutumin bamai satar yara bane mutumin kirki ne, shine Ahmad Tijjani Sabil mai kamfanonin nan wan da ake nuna shi agidajen talabijin, ai ko É—azu dana kawo su makaranta na tarar da motar kamfanin shi tana sauke kujeru dawasu kayan amfani na makaranta,ai kin sa kenan yana da yawan taimako kuma taimakon sa yafi yawa a inda yara suke." "Ahmad Tijjani Sabil." na mai-mai ta sunan a raina ina ta son tuna in da nasan sunan, sai a lokacin na tuna É—azu da safe ake labarai a kansa a gidan tv anan nataÉ“a jin sunan. Naseem yace "Ai nima Daddy yace dai taya min mota in tuka akaina." cikin tsawa nace "Ban ce kada naji wani ya kara min maganar wani Daddy anan ba?, rufamin baki idan ka kara sai na fasa ma baki bari ka gani." Yakubu kuwa ci gaba da zuba yake wan da ma gaba É—aya hankali na baya cikin motar da jikina gaba É—aya. Muna komawa gida nakira *HAM'NAS* Store Complex nace a kawo min motar wasan yara guda biyu da wasu kayan wasa, batare da É“ata lokaci ba motar ShopRite É—in ya iso, a É—akin kayan wasan su aka jibge musu, ihun murna suka sake ganin motocin cikin tsallen murna Naseem yace "La iyin motan da Daddy yace dai taya mana babba." da sauri na mike daga kan kujerar da nake zaune cikin É—akin kayan wasan su, hannayen su duka na riko nadawo na zauna, inajin zuciya ta na min mugun É—aci da kuna a duk san da naji sun furta kalmar Daddy a bakin su, duban su nayi dukan su nace "Kuna ji ko Naseem Nasmah?, shi wancan mutumin ba Daddy'n ku bane baku sanshi ba kuma ku bakuda Daddy, nice Mommy'n ku kuma nice Daddu'n ku bakuga na siya muku mota ba, idan kuka sake faÉ—ar Daddy bazan sake siya muku mota ba, kuma zan sa akwashi waÉ—an nan ma a tafi dasu, baku da Daddy nice Daddyn ku kunji ko?." kai suka gyaÉ—a nace "To maza kuje kushiga motar ku." ai ko da sauri suka ruga in da motar suke suka shiga, ina tare da su a É—akin sai zaga É—akin suke a cikin motar, suna dariya. numfashi nasauke ganin suna cikin farinci sosai, Nasmah ta danna motar ta motar tatafi tsuu zata garu da jikin garu-bango da sauri na mike na tafi da gudu na taro ta, na ciro ta ciki ina faÉ—in "To ya isa haka muje kuyi wanka kuci abinci sai kuma anjima zan sa afito muku da shi can tsakar gida kuyi wasan acan." nayi waje da su. Yau Juma'a da wuri Talatu tagama yi musu shirin makaranta, narako su har sai da motar kaisu makaranta yafita kafin na juya a hankali, gaba É—aya yau jikina baya min daÉ—e a hankali na isa bakin swimming pool na cire takalmata gefe na zauna bakin swimming pool É—in na zura kafafu na ciki, a hankali nake motsa ruwan da kafata ina É—an lilashi ciki, wasu hawaye ne masu É—umi suka zubo kan fuskata banyi kokarin sai da su ko danne zuciya ta daga abun da take jiba, tun jiya nake jin kai na cikin yanayin ina so nayi kuka ko zanji sassaucin abun da nake ji cikin zuciya ta, sai dai ban sami damar yin kukan ba saboda su Naseem, sam bana so nasaka musu rauni cikin zuciyar su, dan aduk san da irin wannan damuwar ta taso cikin zuciya ta zama nake a É—aki nayita kuka, aduk san da sukaga ina kuka sun rika tambaya ta me ya same ni idan nayi shiru ban basu amsa ba ko nace musu babu komai suma sai su fashe da kukan su rungume ni muyita kukan. tabbas ina ganin rauni da damuwa aduk san da hakan tafaru agare su, duk da kuwa kasan cewar su yara wan da basu san komai ba, amma nasan akwan atashi idan hakan yaci gaba da faru zasu tashi da abun a ransu, nasan É—aci da kunar dake tattare da kuncin ganin UWA cikin damuwa game da É—an ta, dan kuwa shike hanani sukuni a koda yaushe. wasu hawaye ne masu zafi da kuna suka cigaba da wanke min fuska cikin jan sheshsheka nashiga faÉ—in "Ummi na kizauna gidan Abba Ummi bazan taÉ“a yafewa kai na ba har idan nayi sana diyyar barin ki gidan Abba, Ummi na zancigaba da yin nesa dake har idan hakan zai sa ki cigaba da zama gidan Abba." kuka sosai ya kwace min cikin muryar kukan nacigaba da faÉ—in "Abba wlh ban ai kata zina ba ban taÉ“a ai kata zina ba, Abba zan cigaba da yin nesa daku har idan hakan zaisa Ummi na tacigaba da zama agidan mu, bana so nayi maraicin uwa batare da tabar duniya ba, Abbu Mamie Ya Masa'ud Auny Rafee'at Aunty Jaleela Nusaiba Fauzaun, kewan ku da begen ku yana hanani sukuni,kullum da ku nake kwana cikin raina, shin haka kuma kuke kewata ina son ku ko da yaushe ina tare da ku a cikin zuciya ta, ku yar da dani wlh Æ´aÆ´ana ba shegu bane, wlh Allah ban taÉ“a zina ba, Allah sarki Inna ta da kina nan da kin faÉ—a musu kalar tarbiyyar da kikayi min wan da ko da agidan karuwai zan zauna bazan yi iskanci ba, bazan yi ba, bazanyi ba, Ya SALEEM Ya SALEEM Ya SALEEM me na tare muku kai da matar ka meyasa zaka rabari da *MAHAIFIYA TA* karabani da ahalina me nayi muku, me yasa zaka sheganta min Æ´aÆ´ana tsaftatattu ka dan ganta su da wani uba wan da bansan ko waye shiba, duk hakan na menene da har sai ka kazanta min Æ´aÆ´a? Æ´aÆ´a na ba kazan ta bane kamar yadda ka faÉ—a Æ´aÆ´ana tsaftatattu ne bazan taÉ“a yafe maka Ya SALEEM bazan yafe maka b...." Kuka ne yaci karfi na nakifa kaina da guiwa na nayi ta kuka kamar raina zai fita. najima sosai zaune a gurin ina ai kin kuka, mai cike da kuna da bakin ciki. da kanshi hawayen ya tsaya badun na tsai da shi ba, sai dai kukan zuci danake, a hankali na mike cikin matsananciyar ciwon kai wan da dakyar nake iya buÉ—e idona duka sabo da zafin ciwon kan, na nufi ciki. direct bedroom na shige kana shiga bathroom wanka nayi nafito na sauya kaya na zo na kwanta bakin gado, karatun Alkur'ani na kunna cikin wayata a hankali nake bin karatun, a sannu narika jin zuciya ta tana samin salama da nutsuwa, a hankali narika jin bacci na fizgata ta, na lumshe idanuna. can cikin baccin da ya É—auke ni da nisan ta baifi na minti 20 ba. najiyo muryar su Nasmah, da gudu suka haye gadon suna faÉ—in "Mommy mun dawo Mommy mun dawo." ida nuna na rumtse da É—an karfi dan har lokacin kai na bai bar yimin ciwo ba, mike wa zaune nayi jin sun zube a jikina na É—ago su ina faÉ—in "Wai har kun dawo? amma dai ba'a tashi ba ko." nayi maganar ina duban agogo, karfe 12 har da rabi,nayi mamakin gani in da lokaci yatafi har haka, ranar yau karfe 12 saura suke dawowa har sun dawo anyi musu wanka an sauya musu kaya. lallai najima ina kuka har ban san lokaci yatafi har haka ba, tausayin kaina ya kamani, É—an guntun kwallar da ke kokarin sauka a idona É—aya nayi saurin kai yatsata na tare shi kana na gyara zama ta ina faÉ—in "Ashe dai lokacin tashin naku yayi, to yaya karatu yau ansha wasa ko." nayi maganar ina shafa kansu. baki Nasmah ta washe ta mike tsaye a kangadon tace "Mommy yau Aunty'n mu tayi mana haka." tarike kugu tare da girgizawa, dariya nayi ina faÉ—in "Au kice yau Aunty rawa tayi muku." "Ba haka bane haka ne". Naseem yafaÉ—a tare da mike wa yarike kugu yasoma tsalle. ido na ware nace "Kai kuce yau kunsha rawa." cikin tsallen yace "Eh ai hadda chocolate ma." tsai da tsallen da yake yayi sai kuma ya dira a godon da gudu yafita sai gashi ya dawo da School bag É—in sa, a tsakiyar gadon ya zazzage School bag É—in sai ga Chocolate masu yawa haÉ—e da littattafan sa sun zubo, da mamaki nace "Yau kuma Talatu kayan zaki tacika muku a jakar." nakai hannu na É—ibo chocolate dasuka kai guda biyar kala daban daban, ga kuma wasu a gaban sa, da É—an mamaki nake kallon su dan asanina babu kalar waÉ—annan chocolate É—in acikin kayan cime-cimen su kalar nasu ba irin wannan bane. "Kai Naseem a ina ka samo waÉ—an nan chocolate É—in?." nayi maganar ina duban sa, da sauri Nasmah tace "Nima akwai nawa." ta dira agadon da gudu tayi waje, Naseem ko bai bani amsa ba sai kokawar buÉ—e laidar chocolate É—in yake. ta shigo da school bag É—in ta itama ta zazzage, nace "Kai wai waya baku wannan abun haka, Talatu Talatu." nashiga kwaÉ—awa Talatu kira dan na fara tunanin ko rikici sukayi mata gun shirya su tabuÉ—e wani katon É—in chocolate É—in daban. Naseem da yakai Chocolate É—in baki ya kutsura yana É—aga kafaÉ—a alamun yana jin daÉ—in abun yace "Daddy yace mucinye wannan duka dai kaya mana wani." "Ai yace idan ka kaiÉ“a min baye kaya maka ba ni de bani da yawa." cewar Nasmah tana kai wan da ta É“are baki. Ido da baki na waro da mamaki tuno wan da suka taÉ“a kiran sa da Daddy a makarantar su nace "Wani Daddy mutumin nan ko?, a ina kuka san shi dan gidan ku da har zaku rika ce masa wani Daddy." Naseem daya cika chocolate a bakin sa yace "Ai Daddy yace kuma dai jo ya auke mu ya kai mu can guyin kifi babba." cikin tsawa nace "Bana ce muku kada wani yasake baku abu ku karÉ“a ba? ashe bakuji ba so kuke nazane ku ko?, bana ce muku nice Daddyn ku nice Mommy'n ku ba, shi ba Daddy'n ku bane, baku san shiba shima bai sanku ba, bakuda Daddy nice Daddy'n ku, kuna jina dai ko?." nariko kunnuwan su ina jijjigawa a hankali, suka gyaÉ—a kai. shiru nayi tare da komawa na jingina bayana da jikin gado jiki a sanyaye nashiga maganar zuci "Kuhi hakuri Æ´aÆ´ana ni zan cigaba da zame muku uwa kuma uba a duniyar na." jin kwalla nakokarin zubomin nayi saurin dakatar dashi... A ranar nasa aka kawo musu chocolate dawsu kayan makulashe aka kara kan wan da yake gida. washegari ranar asabar bamu wuni a gida ba yawon guraren shakatawa muka tafi, ni Faty Naseem Nasmah da kuma Talatu, sai direba. sai yamma muka dawo niki niki da kayan makulashe, washegari ranar Lahadi ma muka kuma fita, shima sai yamman muka dawo a part É—in su Inna wuro muka yada zango sai bayan isha muko koma side É—in mu, ai ko muna shiga su Nasmah suka É“ingire da bacci. koda gari ya waye dakyar nata da su Talatu ta tafi da su dan yimusu wan ka da shirin makaranta, dan tare jiya muka kwana da su. kamar kullum na rakosu muna É—agawa juna hannu suka fita. ina komawa ciki wanka nayi nashirya cikin les copie colour da É—an ratsin gold ajiki, da misalin karfe 10 da rabi nasauko kasa da mayafi akai na sai Æ´ar karamar jaka mai É—auke da wayoyina da wasu Æ´an kuÉ—i dana saka ciki, dinning area na nufa, in da na tadda Zulai tagama shirya komai na breakfast, a É—an gaggauce nayi breakfast É—in, ina yi ina duba agogo, dan fita zamuyi da Bappa zuwa asibitin da ake ginawa dasunan Inna ganin yan da ai kin ke tafiya, ina saurin ne dan jiya nace mishi karfi goma da rabi zamu tafi nasan kuma yanzu haka yagama shiri ni yake jira. koda na fita a kofar masallaci dake ta nan cikin gida na taddashi zaune, na karaso in da yake tare da gaida shi, daga nan muka shige mota muka nufi asibitin. masha Allah asibiti yayi kyau saura kaÉ—an a kammala aiki, bamu bar asibitin ba sai wajen karfe 12:20pm nacewa Yakubu muwuce makarantar su Nasmah mu É—auko su. Abakin get É—in makarantar Yakubu ya faka mota yafita da sauri yana faÉ—in "Bari naje na fito da su". yayi cikin makarantar da sauri, muna nan zaune can yafito da sauri kamar zai kife kasa yakaraso gefen da nake yace "Hajiya wai an zo an É—auke su." ido na waro da mamaki nace "Wa yazo ya É—au kesun bayan kai muna tare da kai ina ce kai ne me zuwa É—aukar su." Bappa yace "Zancen banza kai wani direban akayi musu sabo ne da zaizo É—aukar su? ko dai bakaji abun da suka faÉ—a da kyau bane?." yace "Wlh haka mai gadin yafaÉ—a Bappa." da sauri Bappa ta buÉ—e motar yafita ai ko nima da sauri nafita narufa masa baya har ina haÉ—awa da sassarfa. babu kowa cikin makarantar sai mai gadi da masu kula da tsaftar makarantar sai shara da goge-goge suke, hankali tashe Bappa ke tambayar mai gadi, mai gadin yace "Ai ko minti goma basu da tafiya ba duk É—azu muna tare da su anan da wasu É—aliban mota tazo tafaka nan bakin get suna ganin motar suka zuba a guje zuwa gurin motar suna murna, da naso hanasu dan ganin ba É—aya daga cikin irin motocin da ake zuwa É—aukar su da shi bane, to ganin yan da suke ta murna sukayi gun motar a guje yasa nayi tunanin É—aukar su a kazo, dama badaga gida akazo É—aukar su ba!." maigadi yakarashe maganar yana buga kirji. Yakubu da gumi yafara keto mishi kamar zai fashe da kuka yace "Ina ni ke zuwa É—aukar su kuma gani a gaban ka sai kuma hajiya wata rana,ko mutumin yasako irin fuskata ce ya zo." Bappa yace "Amma kuwa abun da mamaki amma ya kamata lokacin da kaga ba É—aya daga cikin motocin da ake zuwa É—aukar su da shi bane yazo kama yayi kaje kaga ko waye ne,amma wani abun mamakin da kace wai sun je gurin motar da gudu kuma suna murna to ko wani ne daga gida yazo É—aukar su tun da sun san mun fita har da direba?." ni dai kasa magana nayi sai É“ari da jikina yake cikin matukar tashin hankali tuni idanuna suka kawo ruwa kan kace me hawayen suka fara sauka. murya na rawa Yakubu yashiga tafa hannu da salati yana faÉ—in "Dama ance yanzu masu garkuwa da mutane sun canza salo akwai wani abun da suke yi sai dai kaga mutum na ta binsu kamar ya sansu harsu tafi da shi, wayyo Allah Naseem da Nasmah ko dai sune." cikin gwalalo ido mai gadi yace "Wayyo Allah nashiga uku wayyo ai kina shikenan dama ance idan aka sami matsala to abakin ai kina, ashe dama tsarin da masu garkuwa da mutane suka fito dashi kenan? shi yasa yarannan sukayi ta tsalle kamar doki suka ruga in da motar take, ashe jansu ake taciki kamar kuran karfe." É“arin jikina ne yakaru yayin da zuciya ta ke bugawa da karfi gudun hawaye na yakaru. Bappa yace "Kai ya isa haka Falyakum khairan au yasmuq, in sha allahu babu abun da zai faruku muje gidan mugani wata kila daga gida ne akazo aka É—auke su tun da sunsan bama gidan." yadube ni yana cigaba da faÉ—in "Kice Innalillahiwa'inna'ilaihirraji'un." kalmar nashiga nanatawa kana muka juya gun mota, muka bar maigadin nan tsaye yana ta rafka salati dafaÉ—in shikam yau yasan ai kin sa yazo karshe har in sace yaran akayi. acikin mota Bappa yarika zuba addu'o'i yakuma hanani kukan danake shirin yi yace nayi ta faÉ—in Innalillahiwa'inna'ilaihirraji'un. a haka muka isa gida. Muna isa Yakubu yayi hon maigadi ya wangale get yana kokarin wucewa parking lot nace "Ka sauke mu anan." dan gani nake kamar motar bata tafiya da sauri tsabar tashin hankali. tun kan ya dai-dai ta parking muka fito daga motar maigadi yakaraso yana mana sannu batare da dukkanmu mun amsa ba Bappa yayi saurin cewa "Wayaje ya É—auko su Naseem a makaranta a cikin ku?." maigadi yace "Gaskiya babu wan da yaje É—auko su dan tun da kuka fita ma babu wan da yafita, yau kam sunsha zama a makaranta Yakubu yayi hanzarin zuwa É—auko su." "Innalillahiwa'inna'ilaihirraji'un an ce anzo an É—auke su kuma kace ba wan da yafi tun fitar mu an sace su kenan." nayi maganar tare da fashewa da kukan da Bappa ketasa ni danneshi, nacigaba da faÉ—in "Ina suke ina suka shiga waya É—auke su.". maigadi ya walalo ido tare da faÉ—in "Iye! ansace su!." Bappa yace "Ka tabbatar da babu wan da yafita." yace "Wlh babu wan da yafita tun fitar ku ina bakin get É—in nan........! Mommyn Twins ce 8/19/22, 10:55 - Ummi Tandama😇: An buÉ—e murfin motar, baya na É—an yi da sauri dan kaÉ—an ya rage marfin ya bige ni, kasan cewar nazo daf da motar sosai. da sauri na É—ago dan ganin wan da ke cikin motar, ido na waro da É—inbin mamaki ganin mutumin da su Nasmah suke cewa Daddy ne, tsayuwa ta na gyara ganin yazuro kafar sa waje yafito daga cikin motar,baki na buÉ—e cikin masifa ganin yan da yayi kusan bige ni da murfin motar sa, "Malam ya haka baka ganine?." nayi maganar ina yi masa kallon sama da kasa. tsayuwar sa ya dai-dai tare da mai da murfin motar ya rufe, kana yashiga nuna min yatsa tare da kaÉ—a yatsar yasoma magana. "A kan wani dalili zaki rika birkita wa yara Æ™waÆ™walwar su, kinyi yunkurin sauya musu School abaya, ba'a baki dama ba shine kika ajiye su a gida tsawon sati guda, sannan kika sauya musu Makarantar, ilimi kike so su samu ko kuwa birkita musu Æ™waÆ™walwa kike son yi, kada ki kuma yunkuri da tunanin sauya musu makaranta kan wani dalilin ki mara amfani, idan kuma ba haka ba." sai yayi kwafa tare da kaÉ—a yatsar sa. kamar daga sama nake jin maganar nasa mamakin sa da furucin sa suka sani gyara tsayuwa ta ina yi masa kallon kacika mai karfin hali. "Dakata malam." nafaÉ—a ina É—aga masa hannu, kana nacigaba da faÉ—in. "A kan dalilan su Æ´aÆ´ana ina da ikon yin komai da su, dalilina mai amfani, kada ka kuma cewa dalilina bashi da amfani tun da baka sanshi ba, Æ´aÆ´a nawa ne nike da ikon yin komai kansu, malam kafita daga rayuwar Æ´aÆ´ana kana ta yau darar su da danganta su da kai, da suna mai kama da uba, Æ´aÆ´ana basu da uba kuma basa bukatar uba domin bazai yi musu amfanin komai ba, rayuwar su a haka tafiye musu rayuwa da uba sau dubu dan bashi da wani amfani a gare su." sassauta maganar da nake nayi tare da haÉ—e hannaye na biyu kana nacigaba da faÉ—in "Dan Allah kafita daga rayuwar Æ´aÆ´ana kada ka yaudare su da wannan kalma ta uba, dan basu da uba kuma basa bukatar uban, kuma ba shegu bane Æ´aÆ´ane tsaftatattu mafiya daraja." Afusace yashiga matso ni, ganin yan da yanayin sa ya sauya gaba É—aya, sai na shiga ja da baya, shiko maso ni ya cigaba da yi tare da nuna ni da yatsa, yana huci kana yasoma magana cikin É—aga murya "Idan kika sake cewa basu da uba sai ranki yayi mummunar É“aci, idan kika kuma sako kallamr yaudara sakani na dasu!..." sai yayi kwafa tare da kaÉ—a yatsar sa alamun gargaÉ—i, mamakin ganin karfin halinsa muraran nake, wai ni da Æ´aÆ´ana ake nuna min iyakata a kansu, bil hakki da gaskiya yake maganar dan kuwa fuskarsa ta nuna, niko baya na kuma ja ganin yan da ya matso ni sosai yana maganar kamar zai kai min hannu, wani irin kallon shekeke nabisa da shi sannan na ce "Idan ba yaudara bace mene ne, kana cusawa yara abun da babu shi, cikin rayuwar su, ina sanar maka da hakan ne sabo da matsaltawan ka kansu, na dai faÉ—a maka kafita daga tsafgar Æ´aÆ´ana idan kuma ba haka ba zan sa ayi maka gargaÉ—in da zaka fi fahimta." ina kai wa nan najuya. Shan gaba na yayi a fusace cikin muryar da yake nuni da tsantsar gargaÉ—i ya ce "Yazamo na karshe fitar kalmar nan daga bakin ki, idan kika sake kika sake furta kalmar durkuso cikin rayuwar su, bazan sa ayi miki hukunci ba ni zan yi miki hukunci da kai na! ki sake nanata kalmar basu da uba kigani!." yayi maganar cikin fusataccen amon sauti, a zaburi namatsa gefe dan maganar nashi ta shige ni rabon da ayi min ihu da tsawa irin haka har na mance, shiyasa abun yazo min a sabo. ba zato naji kafata ta ta dama ta wuce cikin abu kamar rami, da sauri na juyo sai kawai na tafi luuu gaba É—aya, idanuna na rumse da karfi ina jiran najini a kasa, sai jina nayi zundum cikin ruwa, kara na Æ™walla wan na hakan yayi sana diyyar wucewan ruwa cikin bakina, fafutukan niman numfashi nashiga yi, da niman ceton kaina, duk buÉ—e bakin da zanyi sai ruwa ya wuce ciki, nayi-nayi na iya mike wa tsaye na kasa, duk da kuwa zurfin ruwan idan zan shiga da kafata iya kirji na yake zuwa min. Shiko Ahmad da sauri ya faÉ—a cikin swimming pool É—in ganin yan da ta ke bubbuga hannu da yin sama da shi da alamun niman ceto. hannu na ya ruko da karfi ya É—ago ni yamikar da ni tsaye. ruwan da ke kunshe cikin bakina dana ki haÉ—iye shi dan cikar da ciki na yayi, na furzar da shi tare da sauke tagwayen numfashi, ina damke cikina da ruwa yacika shi, a wahalce na na É—ago hannuna É—aya na share fuskata tare da tattaro gashi na daya rufe min fuska, na mai da shi baya, ida nuna na sauke kansa, dai-dai lokacin daya kai hannu ya share ruwan dake fuskar sa, sai a lokacin na lura ruwan dana furzar daga baki na a fuskar sa na fesa. shima idanun sa a kai na tun daga gashin kaina yake bina da kallo har kasa, kasan cewar rana ya taso ya haske cikin ruwan ana iya kallon abun da ke kasan ruwan. dogon tsaki na ja dan nakasa magana tsabar haushi, bugu da kari yan da cikina ya cike tam da ruwa. a hankali na soma tafiya cikin ruwan har na isa bakin gaÉ“ar gun matattakalar shiga da kuma fita daga cikin swimming pool É—in, a sannu na soma hawa maganar sa na jiyo, "Ki tsaya a taimaka miki kirage ruwan da kika sha." cigaba da haurawa ta nayi batare da waige ko tsayu ba, ina karasa fita da sauri nayi hanyar part É—ina jin zuciya ta na tashi, cikin sauri na shige cikin side É—in direct sama na haura, ina shiga bedroom É—ina da sauri nashige bathroom, ai tun kan na karasa bakin toilet nafara sheka amai tsakiyar bayin, zallar ruwa narika aman sa. da kan sa aman ya tsaya kamar yadda yazo bazato ba sammani, numfashi narika sauke wa ina tallafe da cikina da yanzu nake jin sa wayam, sai dai É—an murÉ—ar da yake min. a daddafe na tsaftace bayin na tuÉ“e kayan jikina da suka jike gaba É—aya na wurgasu cikin wishing machine, nafito doguwar riga mara nauyi na zura, kana na isa bakin gado na zauna ina mai cigaba da sauke numfashi, tsaki narika ja a-kai-a-kai tsabar haushin da nake jin kaina ciki, har lokacin kasa iya furta komai nayi. idan na tuna ruwan da na hambuÉ—a a cikina sai naji kamar nayi ihu, sauki na ma É—aya jiya-jiyan nan nasa aka fidda ruwan dake cikin swimming pool É—in, aka wanke cikin sa a ka kuma zuba wani, ban kuma yi amfani da shi ba. wani dogon tsakin naja yayin da na kai bayana na kwanta kan gado. mamakin karfin hali da takaicin mutumin nan suka rika zuwar min, wai ni yake yiwa gargaÉ—i kan Æ´aÆ´ana, ya kuma yi sanadiyyar faÉ—uwa ta cikin ruwa, badun kwanana na gaba ba wata kila da yanzu ana kan shirin kai ni makwanci. Dole nasa jami'an tsaro cikin lamarin dan ban amin ta da mutumin nan ba, awani dalili zai rika shiga min cikin gida kai tsaye har yarika yimin barazana kan Æ´aÆ´ana. Mikewa zaune nayi tare da É—aukar waya ta, number Mr Aliyu nakira wato P.A na, ko da ya É—aga bayan mun gaisa na É—aura da faÉ—in "Mr Aliyu ina so a saka min jami'an tsaro a gidan nan." da sauri ya ce "Madam meke faruwa akwai matsala ne?." yayi maganar cikin nuna damuwa sosai kana yaci gaba da faÉ—in "Ai Madam tun farko shiyasa nace azuba jami'an tsaro gida kamar wannan dole sai da manyan Security masu rike da bindiga, kikace abar mai gadi kaÉ—ai ma ya isa, ina kuwa zai isar wa gida kamar wannan, yanzu kuwa zan fita in sha Allahu anjima zamu zo da su." na ce "To Allah ya kaimu." nakashe wayar, ina katse kiran kiran Bappa na shigowa, na daga da sallama daga cikin wayar Bappa ya ce "HAMDAH ko kina bacci ne?." na ce "A'a ba bacci nake ba Bappa." ya ce "To kizo yanzu maza." da sauri na mike jin yana faÉ—in haka ya kashe wayar. cikin hanzari na nufi side É—in su Bappa da sauri na dan Bappa bai taÉ“a min irin wannan kiran ba nasan komai akayi akwai wata masalar, da ire-iren waÉ—an nan tunanin nashige cikin side É—in. turus naja na tsaya yayin da jikina ya kama É“ari ganin Yakubu durkushe yana kuma rungume da uniform É—in su Nasmah, cikin tsanani tashin hankali na karaso cikin parlour'n gaban Yakubu natsaya cikin rawar murya da kuka keson kwace min na ce "Ina yara na?!." nayi maganar cikin rawar murya sosai tuni hawaye yacike ido na. Bappa da ke zaune kan kujera ya dube ni tare da faÉ—in "Zo zauna nan HAMDAH." yanu na min kujerar da ke kusa da shi, ban iya bin umurnin Bappa ba dan kuwa hankali na yakai kololuwa wajen tashi, duba da yan da Yakubu yake É“ari yakuma rungume uniform É—in gam-gam. Inna Wuro ce ta mike tazo taruko faÉ—ata ta jamyo ni ta zaunar da ni kan kujerar, tuni hawayen da suka cuko idona suka fara zuba. Bappa ya girgiza kai yana faÉ—in "Muma mun shiga irin yanayin nan da kika shiga a yan da yashigo mana kamar an rakoshi a guje, tam bayar da na fara mishi shine ina yaran suke ganin uniform É—in su a hannun shi, da kyar ya iya ba mu amsar suna nan kuma suna makaranta, yaji tsoron ya tinkare ki kai tsaye shiyasa yazo nan." kai Yakubu yashiga gyaÉ—a wa yana É—an rarrafowa da guiwar sa yana kuma faÉ—in "Dan Allah dan Annabi Bappa Malam ka rokar min afuwar ta wlh duk yan da naso na hana faruwan haka bai yuwu ba, wlh fin karfi aka nuna min muraran." Bappa ya katse shi ta hanyar É—aga masa hannu ya ce "Ya isa." kana Bappa ya juyo da kallon sa gare ni ya ce "Lokacin da suka fita zai kai su makaranta a hanya suka haÉ—u da Ahmad Tijjani Sabil ya sai da su, yake tambayar su ina zasuje ganin ba hanyar makarantar su suka nufa ba, sannan kuma ga wata uniform É—in daban a jikin su, to shine shi Yakubun ya shai da masa in da zasu, shikuma Ahmad yace kada ya kuskura ya kaisu wannan makarantar yawuce ya kaisu wan can makarantar su, to dai a takaice tare suka tafi da shi wancan makarantar da aka cire su yasa aka basu wani uniform, yakuma tuÉ“e musu najikin su shine yabashi wan da yacire musun yace ya mai do shi gida, to shine ya dawo hankali tashe yakuma ji tsoron yaje ya tinkare ki da batun shine ya zo nan, kafin na kira ki sai da na kira shi Ahmad É—in sabo da ina da lambar sa dan ranar da yazo nan na karÉ“i lambar sa, ashe dai zatayi amfani gaba akuma irin wannan ranar,shine na kira sa dan ji dalilin sa na yin hakan, ya bani tabbacin dalilin sa na yin haka, kuma na gamsu, yace yawai ta canza musu makaranta a karancin shekarun zai iya birkita musu Æ™waÆ™walwa gara abar su idan suka gama can É—in kan lokacin sun daÉ—a wayo sai suyi gaba, kuma nima nayi nazari naga hakan yafi abarsu a can É—in, nayi masa maganar dalilin ki na canza musu makarantar yace za'a kara tsaro sosai babu wata matsala." Yakubu da tun da Bappa ya soma maganar yake ai kin gyaÉ—a kai da buga bayan hannun sa cikin É—aya tafin hannun sa, yayi kalar tausayi, Bappa na gama maganar shima ya É—aura da faÉ—in "Wlh tallahi Hajiya na rantse miki da Allah, ba laifi na bane, na dage wajan ganin ba'a kuma samin wata matsala ba kamar yadda nayi miki alkawari, wlh Hajiya dana buÉ—e baki zanyi masa musu dawani yafito daga cikin motar sa, ya shake ni sai da naji kamshin kabari, shi ya hana mutumin da yanzu na sheka, ki gafar ceni Hajiya ki tai maka kibar ni a bakin aiki na." Numfashi na sauke jin akasin abun da nake tunani yafaru a kansu, dan Ni nagama tunanin hatsari sukayi sun mutu shine yakawo kayan su gida. duban Bappa nayi ina shere hawayen fuska ta nace "Yan zu Bappa ka amin ce da abun da yafaÉ—a kenan?, to shi ina ruwan shi da su me ya shafe shi da lamarin su da har zai rika shiga, har fa Daddy yake cewa surika ce mishi meye gamin sa da su." murmushi Bappa yayi irin tasu na manya kana ya ce "To in ban da abin ki HAMDAH ai wan da ya nuna yana son naka yagama yi maka komai a rayuwa, kuma da kike cewa yana shiga lamarin su basu kaÉ—ai ba lamarin koma waye yana shiga, idan baki mance ba na taÉ“a baki labarin sa nazu wa rugar mu da yayi, muma ba lamarin mu yashiga ba yakuma jiÉ“anci lamuran mu, yayi silar magance mana wutar fitinar da take ta kunno mana, ko jiyan nan da daddare munkalli labarai gidan TV wasu iyaye sun fito suna mika masa godiya kan gudumawar da ya bada kan Æ´aÆ´an su, su iyayen ma basu ma sani ba Æ´aÆ´an ne suka dawo gida suke faÉ—a musu alkhairin da yayi musu, a makarantar gwamnati suke karatu ya cire su ya mai dasu na kuÉ—i, sannan kin ce meye gamin sa da su, ke da kike taimakon bayin Allah meye gamin ki da su?, ai shi tai mako basai wan da kasani kake taimaka masa ba, duk wan da Allah ya sa da rabon sa yafaÉ—o ta kansa sai ka taimaka masa ladan ka na gurin Allah, shiya sa Allah ya halittomu kala biyu mai kuÉ—i da kuma talaka hakan kuma jarabta ce, idan kai me kuÉ—i ne kayi kokarin cin jarabawar da yayi maka, wato kajikan na kasa da kai, ka kuma tsare dokokin Allah, to da yardar Allah babu shakka zaka shiga aljanna ta sanadiyyar jaraftar ka da yayi da arziki, idan kuma kai talaka ne, karike talaucin ka kabi dokoki Allah, kai ma zaka wuce aljanna da yar dar sa. shi tai mako ba sai wan da kasani kake yi masa ba. kiran sa da sunan uba kuma da suke yi, ai duk É—a nagari shike daraja nagaba da shi yakira sa Yaya wan da ya haifesa kuma yakira sa da sunan uba, wan da yayi jika da shi yakirasa da Kaka, abun alfahari ne É—anka yazamo daga cikin irin waÉ—an nan Æ´aÆ´an, ba ai bu bane dan sun kirasa da suna Daddy tun da yakai ya haife su, zaki so ace Æ´aÆ´an ki suna da rashin kunya ko basu da tarbiyya?." Shiru nayi batare da nace komai ba. murmushi Inna Wuro tayi,dan ta fahimci in da maganar tawa ta dosa, kana tace "HAMDAH kenan ai laifin wani baya shafar wani." kana ta kawar da zancen da faÉ—in "Sai kiyi wa Yakubu hakuri ya dai na wannan tafa hannu da É“arin jikin da yake." da sauri Yakubu ya daÉ—a rarrafo wa gaban mu yace "Whl Innar Gida kada kiga shakar da mutumin nan yamin, tsaro biyu ne suke girgiza ni a jikina, tsoron kada Hajiya ta kore ni daga ai ki na, da kuma tsoron wannan basamuden mutumin da suke tare da Ahmad Sabil daya makuren makogaro." yayi maganar yana É—aga wuyar sa da nuna mana in da ya shako san. dariya duk sukayi ban da ni dana murmusa kawai. na yar da da dukkanin maganar da Bappa yayi, sai dai inajin abune me wuya na iya jure wa dajin kalmar uba na fita daga bakin su Naseem. Bappa yacewa Yakubu ya tashi ya tafi anjima yaje ya É—auko su a makarantar. ya mike yana zuba godiya yayi waje. Haka su Bappa sukayi ta jana da hira bani na bar side É—in ba sai wajen karfe 12, gani lokacin dawowar su Naseem yayi nayi musu sallama nakoma side É—ina. komawa ta bada jimawa ba su Nasmah suka shigo a guje, kalmar da suka fara furta min shine Daddy'n su ya ce gobe zai zo ya É—auke su a mota. ban iya ce musu komai dan ko na faÉ—an ma abanza ne... A É“angaren Ahmad Tajjani Sabil, tun da yabar gidan tuki yake kamar mai koyon tukin, a haka ya iso bakin wani katafaren get me girma da tsaruwan gaske, yayi hon batare da É“ata lokaci ba a ka wangale masa katafaren get É—in, a sannu ya dannan hancin motar sa ciki, ya ilahi ya lillahi gida ne mai matukar girman gaske, alkalami na bazai iya zana girma da tsaruwan gidan ba, FAN'S na barku ku hasasho da kanku. a hankali ya isa parking lot in da motoci da suka kai guda biyar ke jere agun ya yayi parking, a sannu ya buÉ—e motar yafito, daga can wasu matasa guda uku suka iso in da yake da sauri, suna faÉ—in "Barka da dawowa master." hannu kawai ya É—aga musu tare da yi musu murmushi, batare da yace komai ba, yasoma tafiya a hankali ya iso ba kin wata kofa, jiki ba kwari ya tura kofar yashiga da sallama É—auke kan laɓɓan sa. wata kyakkyawar mace fara Æ´an duma-duma ce ke zaune cikin katafaren kayataccen parlour'n, tana ganin sa ta ajiye wayar dake rike a hannun ta, ta mike da sauri, ta nufo shi da É—an sassarfa, tun kafin ta karaso ya buÉ—e hannayen sa ta shige cikin jikin sa ta rungume shi, hannayen sa ya haÉ—e yazagaye bayan ta tare da manna mata kyakkyawan sumba a goshi, ido ta lumshe tare da buÉ—e wa lokaci guda, kana ta É—ago kanta ta mannan masa kiss a kumatu. yan da tayi shima haka yayi, ya lumshe idon tare da kuma buÉ—e wa, itako hannun ta tayi sama da shi ta sakalo wuyan sa taÉ—an langwaÉ“ar da kai gefe kana ta soma magana cikin shagwaÉ“a "Aboki ka mance da nine?." ido ya waro da alamun maganar tata tayi girma, baki ta cuno gaba tace "To shine nayi ta kiran ka a waya baka É—aga ba, kuma baka neme ni ba tun da ka fita, ni da na nime kan kaki amsa kiran." maganar take cikin shagwaÉ“a kamar zata fashe masa da kuka. kuma tun ta ya kama yaÉ—an ja kana ya ce "Na isa naki É—aga kiran ki kinga wayar da na fita da ita É—aya wayar tana gida ai." yayi maganar yana nuna mata wayar dake rike a hannun sa. murmushi tayi tare da faÉ—in "Ai har da nayi fushi." hannun sa ta ruko tana faÉ—in "Toho muje kayi wanka." ta janyo hannun sa sukashi ge cikin wani kayataccen bedroom, suna shiya da kanta ta tuÉ“e masa kayan jikin sa, boxes kaÉ—ai ta bari takuma janyo hannun nasa sukayi cikin bathroom. Ta taimaka masa yayi wanka suka fito É—aure da towel a kugun sa. lokacin an fara kiraye-kirayen sallar azaha jallabiya ya zura ya jasu sallah nan cikin É—akin, ko da suka idar, zaman sa ya gyara ya jingina da jikin bayan sa da jikin garu-bango yana lazumi, ido taÉ—an tsura masa kana sai kuma ta mike ta fita jim kaÉ—an ta dawo É—auke da tray mai girma a hannun ta, a gaban sa ta dire, kana tashiga buÉ—e kulolin da suke kan tray'n har guda uku, wani daddaÉ—an kamshi ne suka fara tashi daga cikin kulolin, nan da nan É—akin ya kaure da kamshin lafiyayyun girkin. tazuba cikin plt tare da saka cokula guda biyu, ta gyara zaman ta da kyau ta maso gaban sa, in da ta saka plt É—in a tsakiyar su, suka rika cin abincin gwanin ban sha'awa sunayi suna É—an taÉ“a hira da zolayar junan su, a haka har suka kammala, takwashe kayakin ta mai da su kitchen, ko da ta dawo ta taddashi ya koma gado, yana É—an danne-danne a waya. kimsa in da suka É“atan tayi kana tazo bakin gadon ta zauna, dai-dai in da kansa yake, ta gyara zaman ta da kyau ta É—ago kansa ta É—aura kan cinyar ta, yayin da ta cusa hannunta cikin sumar kansa tana É—an yamutsa shi cikin tsalon sa mutum yayi bacci. aje wayar dake rike a hannun sa yayi, kana yayi sama da hannun sa ya shafi gefen fuskar ta, a hankali cikin muryar jin baccin da yafara ziyar tar sa, ta sanadiyyar abun da take masa, ya ce "Kawa nayi bacci kenan?." kai ta gyaÉ—a tare da faÉ—in "Eh nasan ka gaji." numfashi ya sauke kana yayi kasa da hannun sa yadaÉ—a gyara kwanciyar sa da kyau a hankali yashiga sauke numfashi. batare da É“ata lokaci ba bacci yayi gaba da shi da taimakon yan da take sarrafa gashin kansa da wasu sassa na jikin sa. sai da ta tabbatar da baccin nasa yayi nisa, sannan ta É—aga kansa a hankali ta janyo pillow ta saka masa kana ta mike tafita, domin sanya ido kan aikin da masu aiki suke gudanar wa a gidan... Da misalin karfe uku da rabi ya farka bathroom ya faÉ—a can yafito ruwa na É—iga daga jikin sa da alama wanka yakuma, gaban wardrobe ya tsaya yaciro kaya wani dakakken yadi ne wan da daganin sa ma kasan bana wasa bane sai dai manyan kam. bayan ya saka ya isa gaban mirror turo kofar a kayi daga cikin mirror yazubawa kofar ido, lallausan murmushi ya sake wan da sai da kumatun sa suka lotsa, lokacin da suka haÉ—a ido da ita tacikin mirror, baki ta É—an turo gaba kana ta tako zuwa in da yake, ta É—aura hannun ta kan hannun sa daya É—aura kan turare yana kokarin É—auka, ta amshi turaren sannan ta dube shi tare da faÉ—in "Shine zaka yi wanka baka neme ni na taya ka bako?." kai yaÉ—an langwaÉ“ar sannan ya ce "Nayafe miki ai nasan kin sha wuya wajen sani yin bacci." turaren ta É—ago tafara fesa masa a jiki sannan tace "Babu wani wuya gun ai kin lada ni dai wayo kayi min ka hanani samin wannan ladar." "Kinfa tara ladan nan da yawa amma rabawa zamuyi ko?." yayi maganar cikin tsigar zolaya yana kuma jan kuma tun ta. kafaÉ—a ta make ta ce "Naki wayon naka yafi nawa yawa ai." dariya suka sakar wa junan su. sai da ta fisa masa turaruka wajen kala uku kana ta gyara masa zaman hular kansa, ta ce "Kafito sosai fa." "Haba original mirror ai ba ma sai naga wannan jebun ba." yafaÉ—a yana nuna mirror. murmushi tayi kana taÉ—an tsura masa ido sai kuma ta ce "Aboki me ke damun ka?." tayi masa tambayar cikin nuna tsantsar kulawa. da sauri ya ce "Wani abun kika gani ne, to ni kuma me zai dame ni bayan ina da ke." ya kai bakin sa kan goshin ta tare da mannan mata kiss. numfashi ta sauke tare da É—an yin shiru tana nazartar yanayin sa, kana ta ce "To shike nan muje na rakaka katafi masallacin gashi ana kan kiran sallah." Hannun ta ya damke cikin nasa cikin son kawar mata da shakkon dake hangowa kan fuskar ta ya ce "Babu komai fa." da sauri ta katse shi da faÉ—in "Ban kuma cewa komai ba fa muje katafi masallaci......"! Mommyn Twin ce 8/19/22, 10:55 - Ummi Tandama😇: Nan nake shai da masa bukata ta nakan canza su Naseem makaranta. shugaban makarantar nasu yace "To ba bubu da muwa amma dan Allah muna so musan dalilin da yasa ake son sauya musu makarantar ko kuma makarantar tamu babu koyo ne yan da ya kamata?". nace "Ko kaÉ—an ba haka bane ba kawai dai ina so ne na canza musu makarantar ba wai kodun rashin koyo ba, ai ba za'a ce makarantar ku babu koyo ba, yara suna fahimta sosai, kawai dai yaÉ—an yi nisa ne." yace "To in dai kuwa haka ne to dan Allah kada a ciresu a makarantar gaba É—aya, akwai É—aya makarantar mu dake wata unguwa mafi kusa da ku in dai kina so sai a maida su can É—in, ranar Monday idan suka zo sai ayi transfer É—in su can É—in." shiru na É—an yi cike da nazarin maganar sa, sai kuma nace "To shi kenan a mai dasu can É—in." har munyi sallama zan kashe wayar yayi saurin cewa "Dan Allah Madam a daure a kawo su sai a kaisu wancan makarantar, idan akace an cire su gaba É—aya kokon to zai shiga zukatan iyayen yara zasuyi zaton ko wani matsala ce mai girma aka samu cikin makarantar, tun da bawai barin garin zakuyi ba, zamu iya samun dakilewar customer, adai duba lamarin da kyau Hajiya." "Babu damuwa in sha Allah za'a kawo su sai a kai su wan can É—in." godiya yashiga yi min kana mukayi sallama na kashe wayar. Ina sauke wayar number Ukhtee na kira yayi ta ringing ba'a É—aga ba,nakuma mai da kiran shima har yakusa yanke wa kafin ta É—aga, da sallama. na amsa cikin harshen larabci nace "Oh kai Ukhtee ina kika aje wayar haka ina ta kiranki baki É—aga ba?, ko yanga kike min an ce miki ni saurayin kine." dariya tayi tare da faÉ—in "Saurayi kuma haba dai kedai wayar tana bedroom ne nikuma ina parlour, nama shigo É—aukar abune cikin É—akin naji wayar tana ring, ai da haka zaki ta kira ma ban sani ba, ya kuke ina yarana suke?." "Lafiya lau duk muna lafiya, yaran ki suna can gurin Bappa sunki biyo ni suna can suna damin sa da surutu, ni nagaji da hirar ne nadawo side É—ina naÉ—an huta suna can." larabcin nake ina ta haryaÉ—a shi. dariya tayi jin yan da nake ta kwamusa larabcin, tace "Oh kin dawo kasar ku yaren kasar ku yana so ya korar miki da yaren kasar muko?." nima dariyar nayi tare da faÉ—in "Ashe kin gane inata yi da kyar amma fa su Naseem sunanan da shi a bakin su domin makarantar isilamiyyar su larabci zalla ake, shi yasa yake nan zaune a bakin su." tace "Kai naji daÉ—i wlh gara ai su zauna da larabcin a bakin su, ke kizauna da yaren kasar ku tun da shi kika zaÉ“a." nace "To ya zanyi mahaifa ta dole naso yare na ke ma ba kina son yaren kiba?." tace "Sosai ma." "Oh to shine nima baki so naso nawa yaren." mukayi dariya. hira kukayi tayi sosai da Ukhtee wani maganar idan nayi ita zata gyara min shi dan larabcin bai gama nuna baki na ba. sai can da jinawa mukayi sallama. Yau Monday kamar yan da nasa ba na rako su Nasmah gun mota, Yakubu dake goge motar yayi saurin buÉ—e motar nasaka su ciki,bayani na yiwa yakubu kamar yan da mukayi da shugaban makarantar su idan sun je za'a haÉ—a su da wani domin yayi musu jagora zuwa É—aya makarantar. ina tsaye ina É—aga musu hannu har suka fita... Kai tsaye Yakubu yaÉ—au hanyar makarantar, kamar koda yaushe hira yake da yaran yanata washewa da dariya kamar yan da suma suke ta washe baki. suna isa bakin get É—in makarantar yayi parking yafito, kana ya buÉ—e musu suka fito, suna fita suka shige cikin makarantar direct office suka nufa daga nan aka haÉ—a su da wani malami da zai kai su É—aya makarantar, suka fito tare. suna fita bakin get É—in school É—in, wata lafiyayyi zazzafar mota tayi parking a gefe, tun kan motar ta kakarasa parking Naseem yafara murna yana faÉ—in "Laa ga Daddy yazo laa ga Daddy yazo." Nasmah ma kuwa ihun murna ta sake tare da sa gudu sukayi gurin motar. da sauri ya buÉ—e motar ya fito yaware hannayen sa ai ko da gudu suka shige jikin sa ya rungume su, duk suka saki dariya har dashi, kana ya mike yashiga É—aga su yana cillasu sama sai kya-kya ta dariya suke. sai da yayi wa kowannen su haka har sau uku kana yadire su kasa, Yakubu ya karaso in da suke yana washe baki da faÉ—in "Ranka shi daÉ—i barka da war haka." amsa wa yayi fuska a sake sai dai gaba É—aya hankalin sa na kan su Nasnah da suke ta zuba masa surutu. shima wannan malamin da aka haÉ—o su da shi ya karaso yana faÉ—in "Barka da zuwa yellaÉ“oi." yace "Yau wa, yaya ji da É—aliban?." malamin yawashe baki tare da faÉ—in "Muna kai kam." yace "Masha Allah." malamin ne ya dubi yakubu da kuma yaran yace "To muje ko." yayi maganar yana duban motar su. sai a lokacin Ahmad ya É—ago da kallon sa kan yaran yadawo da shi kan su Yakubu kana yace "Ina kuma za'a je ba makaranta za'a shiga ba?". yayi maganar yana shafa kan su Naseem. malamin yace "A'a zamu tafi da sune É—aya makarantar mu." duban sa Ahmad ya kuma da alamun tabbayoyi É—auke a fuskar sa, kana yace "Wacce makarantar kuma?." yace "ÆŠaya daga cikin makarantar mu ne za'a mai da su." da fuskantar mamaki Ahmad yace "Har sun gama wannan makarantar ne da za'a tura su wata makarantar daban?." kai malamin ya girgiza tare da faÉ—in "A'a ai za'a sauya musu makarantar ne anyi musu transfer can ne." É—an shiru Ahmad yayi kana yace "Malam É—in yana ciki?." kai malamin ya gyaÉ—a tare da faÉ—in "Eh yana ciki." yace "Okay to muna zuwa." yafaÉ—a tare da gyara rukon Naseem da Nasmah a kowani hannun sa guda, ya janyo su suka shige cikin makarantar. Malamin ya dubi Yakubu dake ta washe baki yace "Wai nikam da ma Æ´aÆ´an Ahmad Tijjaji Sabil ne kake kawowa makaranta?." Yakubu ya daÉ—a washe baki yace "A'a Æ´aÆ´an me *HAM'NAS* Company ne fa." "Au Æ´aÆ´an mai *HAM'NAS* Company ne to shi Ahmad Sabil dangin su ne? lallai Allah mai yin yan da yaso yahaÉ—a family guda da tarin dukiya." Yakubu yace "Eh Æ´an uwa ne." yafaÉ—i hakan ne kawai dan bashi da amsar bashi, dan shi kansa bai isa yace suna da dangan taka ko basu da shi ba, a matsayin sa na mai ai kin gidan ba lallai dole yasan dan gin gidan ba, san nan kuma baya so ya disga kan sa gaban malamin, ko ba komai shi ma za'a rika yi masa kallon wani... suna nan tsaye zuwa can Ahmad yafito shi kaÉ—ai batare da yaran ba. ido suka zuba masa ganin yafito shi kaÉ—ai, yakaraso in da suke, duban malamin yayi tare da faÉ—in "Ka koma kacigaba da koyar da É—aliban ka, kai kuma ka koma gida ka dawo da wuri ka É—au ke su." yakara she maganar da duban Yakubu. Yakubu yace "Ranka shi daÉ—e hajiya tace na tsaya sai mun kai su kafin na komo gida." Yace "Kar ka damu kaje ka abin ka." yace To. yashiga mota in da tuni malamin ma yakoma cikin makarantar. shiko Ahmad a hankali ya isa jikin motar sa ya shige ciki... Da misalin karfe 12 a hankali na mike na shige bayi wanka nayi haÉ—e da É—auro al'wala nafito,nashirya cikin wani doguwar rigar atamfa pauda da man lip kawai na goga sai turare dana fesa a jikina, a hankali na isa jikin window labulen window'n naÉ—an janye shi gefe tare da zuge glass. ido na kurawa furannin da suke ta kaÉ—a wa gwanin ban shawa, idanuna na sauke can bakin get jin karar buÉ—e get É—in, da murmushi nake kallon kofar, dan nasan su Naseem ne suka dawo, É—an gimtse annurin fuska ta nayi ganin ba motar kai su makaranta bane wata motar ne daban ta shigo. a sannu motar ta isa ta gyara parking a gefen farfajiyar gidan, an É—au tsawon minti 10 kafin aka buÉ—e motar, ido na waro cikin tsananin mamaki da shiga shoc ganin wan da yafito daga cikin motar, cikin matukar kufula nake kallon sa yayin da yazaga É—aya gefen ya buÉ—e, sai ganin Naseem da Nasmah nayi sun fito daga cikin motar suna ta washe ba ki. "What! me nake gani haka, yaran da nasa a canza musu makaranta domin sa wai bin su yakuma yi?." cikin matukar É“acin rai nasaki labulen da sauri na juya nafita a É—akin na nufi kasa, da sauri na ke sauka har ina haÉ—a step cikin hanzari nakarasa sauka nayi waje da sauri. Suna tsate jikin mota sai zuba masa surutu suke shiko sai binsu da murmushi mai haÉ—e da dariya yake, tun kan na karaso in da suke nashiga faÉ—in "Kai malam wai meye hakan ne, wai meye gamin ka da yaran nan ne kam?!." dai-dai lokacin na iso in da suke, kugu na rike cikin masifa nacigaba da faÉ—in "Meye da lilin ka na wani shishige musu da kake kana ta wani cusa musu wani ra'ayi meye nufin ka da su?." maganar nake a tsai-tsaiye kuma cikin É—aga murya cikin masifa nakuma faÉ—in "Bana bukatar wani ya raÉ“e su da manufa irin naka kagane ko malam?." tun da na fara maganar ido kawai ya zuba min batare da yace komai ba, idanun sa kan lip É—ina, a sannu yaÉ—an yi baya ya jin gina bayan sa jikin mota hannayen sa ya sarkafe a kirjin sa, harshen sa yaÉ—an zuro waje yalashi pink lip É—in sa, har lokacin fuskar sa na É—auke da murmushi wan da dimple suka daÉ—a kawata annurin fuskar sa. cikin kuma É—aga murya na dubi su Naseem nace "Idan baku wuce kun shiga ciki ba na rantse sai na É“aɓɓala yaro anan gurin ku wuce mutafi nace!." nafaÉ—a ina nuna musu hanya. Nasmah tace "Mommy ja mu jo." ido na waro wato ma na jira su kenan sai sun gama abun da suke. shiko wani murmuahi yakuma sakewa. tsayuwar sa ya gyara tare da duban yaran kana ya mai da duban sa kai na sannan yafara magana "Zaki É“alla su?." ya faÉ—a tare da kuma sakin wani murmushi kana ya É—an sun kuya yarage tsawon sa dai-dai tsawon yaran ya dubi ko wannen su yace "Kuje ciki ayi muku wanka kuci abinci ku kwanta ku huta kuyi bacci idan kun tashi kuyi karatu gobe zan tambaye ku karan tun da kukayi kun ji ko?." kai suka gyaÉ—a masa suna faÉ—in "Tom." yace "Yauwa to maza a je ciki." Naseem yace "Daddy dakajo anjima?." kai yagyaÉ—a yana mai cigaba da wannan murmishi wan da kamar da shi aka gina fuskar sa yace "Sosai ma zan zo mana." Cikin hatsala haÉ—e da É“acin ran ganin yau ma kamar na ranar da na same su tare da shi a kofar makarantar su, ina nayi musu magana sukayi kamar basu san ni ba, sai shi da suke ta biye masa suna bashi amsar duk abun da yace musu, bugu da karin bacin raina kiransa da sunan dana hane su a gabana. cikin tsawa nace "Kai Naseem me nace maka waye Daddy'n ka wato bakaji ba ko, ban ce muku kada ku kuma cewa wani Daddy ba, wato duk maganar da nake muku aban za bakwa ji ko, idan naji kasake cewa wani Daddy sai na fasa maka baki,wuce mutafi nace!." ko da nake masifar harlau idanunsa a kai na, sai ya saki wani murmushin gefen baki yayin da gefen kumatun sa na dama ya lotsa, har kuma lokacin yana rike da kafaÉ—ar su. a sannu yaÉ—an sun kuyo yadubi Naseem kana yakuma dubi Nasmah kana yakuma sakin wani murmushin sannan yace "Naseem Nasmah mene ne ma suna na?." suka haÉ—a baki wajen cewa "Daddy Daddy tunan ka." yace "Kai yaran nan to Allah yayi muku albar ka, to maza ku tafi ciki ayi muku wanka kuci abinci maza kuje." ya faÉ—a yana tura keyar su. ai ko da gudu suka yi ciki suna dariya, ganin rainin wayon nasu da yawa yake wato umurnin sa ma zasubi ba nawa ba. nadube shi tare da rike kugu nace "Kai malam kana ji ko, kada ka sake zuwa in da yara na suke kada ka sake kasake zuwa in da suke, kada ka sake cusa musu ra'ayin cewa wai kai Daddy'n su ne, kai ba Daddy'n su bane basuma san ka ba, ni ban gayyaci wani acikin lamarin Æ´aÆ´ana ba,karabu da harkar yara na idan kuma ba haka ba wlh zan É—auki tsatstsauran mataki a kanka, kada ka kuskura ka sake zuwa in da yara na suke, kada ka sake yi musu karya kan abun da ba haka bane, bana kara kan haka dan Æ´aÆ´ana nice kaÉ—ai uwan su kuma uban su, dan Allah malam kada ka sake cusawa Æ´aÆ´ana wannan gurguwar ra'ayin, ka gane ko?!." na karashe maganar da nuna masa yatsa haÉ—e da murguÉ—a masa baki, na juya a hatsale ganin duk maganar da nake madadin ya shiga taitayin sa sai ma daÉ—a sakin wannan murmushin nashi yake. tafiya na soma cikin fushi dan nalashi takwabin yau sai na zane yaran nan tun da har ni zasu gwadan wani yafi ni muhimmanci agurin su har zasu ji maganar sa akan nawa. sai jin maganar sa nayi daf dani "Kece uwan su kuma uban su to ya akayi kenan hakan ta faru, ke kika ba kan ki cikin kenan,faÉ—a min da ma a she mace tana bawa kanta ciki da kanta, dama a she uwa tana bawa kanta ciki ita kaÉ—ai batare da uba ba??." wani irin juyi nayi jin sautin sa kusa dani batare da zato ko sammani ba, maganar yashige ni tamkar shigar shoc cikin jini na, wani irin mugun kallo na watsa masa tare da jan dogon tsaki, najuya na nufi kofar side É—ina da sauri... shiko bayana yabi da wannan murmushin kana ya juya yashige motar sa yaja yabar gidan. Koda na shiga banbi takan su Naseem ba dan nasan koda na yi musu hukuncin danayi niyyar ma bashi zai sa su dai na abun da na hanasun ba, sai kawai nashige É—aki nazube bakin gado, kamar an zabure ni kuma na mike na isa gaban mirror in da wayoyi na suke ajiye, number Yakubu na kira, nafara zazzage masa masifa "Wato Yakubu dana ce kaje ka É—auko su shine bakaje ba kabar wannan É—an rainin wayon mutumin wai Ahmad yake ko wa yaje ya É—au ko su ko?, idan ka gaji ne kafaÉ—a sai a sallame ka." da sauri yatari numfashi na da faÉ—in "Dan Allah Hajiya kiyi hakuri wlh yanzu haka ina hanyar dadowa ne ina ma kokarin kiran ki kenan sanar miki sai ga kiran ki, naje makarantar aka ce min yazo ya É—auke su, ai Hajiya baki sani bama É—azu da zamu kai su sabon makarantar yazo ya mai da su cikin makarantar yace mutafi mu barsu anan." ido na waro da É—inbin mamaki mai haÉ—e da mugun É“acin rai, ban san san da na dakawa Yakubu tsawa ba nace "Dalla malam ya isa ni da kai na nace ayi abu kan Æ´aÆ´ana sannan wani can daban yazo yace ba hakaba kai kuma ka yarda, umurnin sa kabi kenan? ok to ka wuce gidan sa daga nan kaje can yacigaba da baka umurnin!." nakashe wayar rai É“ace, "Lallai ma wato ashe ma ba'a kai su makarantar ba shike nan ya hana ko me?." Afusace na danna number shugaban makarantar yana É—agawa nace "Malama ya zan ce ga abun da nake so sannan kuma wani yazo ya hana kuma ku amin ce, to gaskiya daga yau bazama su sake zuwa makarantar ba ma sun fita kenan." da sauri yace "Ranki shidaÉ—e mahaifin su ne yazo yace kada a canza musu makarantar bawai yin kan mu bane." kashe wayar nayi jin raina yadaÉ—a É“aci. dogon tsaki naja tare da yin kwafa nama kasa cewa komai saboda sabar bakin ciki,sai dai naci alwashin daga yau baza su sake zuwa makarantar ba, zan mai da su *HAM'NAS* International School Of Science And Technology. After 1 week Tsawon sati guda agida suka yishi ranar Lahadi nasa aka kawo musu uniform na *HAM'NAS* International School Of Science And Technology. washegari Monday da misalin karfe 7 aka gama kimsa su tsaf, muna tsaye a parking space, daga can na É—agawa Faty hannu da fito war ta kenan daga side É—in su, nayi mata alama da tayi sauri, ta Kara so da sauri, tace "Ina kwana Adda HAMDAH." murmushi nayi tare da faÉ—in "Lafiya lau antashi lafiya." "Lafiya lau." tafaÉ—a tare da duban su Nasmah tace "Yau yara sun koma School É—in mu." hannun ta Nasmah tarike taÉ—ago kanta tana duban ta tace "Aunty Faty School inku akwai lilo?." Faty tace "Eh har da abun zame-zame da mota mai lilo da doki mai lilo." tsalle Naseem ya tuma yana faÉ—in "Yeee nine zan shiga moto in tuka ku." dariya duk mukayi, na dubi Yakubu dake ta faman goge mota, nace "Dan Allah kabar goge motar nan haka in ba halitta zaka sake masa ba, kutafi haka kada kasa su makara,kuma dai kaji abin da na faÉ—a maka wlh aka kuma samin wata matsalar duk wani hakuri da magiyar ka bazai maka amfani ba." nayi maganar ne cikin jin haushin sa na rannan dan da kyar na hakura da hakurin da yayi ta bani. da sauri ya bar goge motar yabuÉ—e marfin motar yana faÉ—in "Zo ku shiga Naseem, wlh hajiya in sha Allahu baza a sake samin wata matsala ba, wancan rabar ma tsautsayi ne, dakuma ganin shi babban mutum ne a kasar nan shiyasa ban masa musu ba, dan gudun kada yasa a kwashe ni akai ni gidan maza, dan musu da babban mutu awannan zamanin haÉ—ari ne." tsaki naja tare da faÉ—in "Kabari zai kai ka karshen É—auri kenan." najuya naso ma tafiya ina É—agawa su Nasmah hannu da cigaba da faÉ—in "Kadai ji abun da na faÉ—a maka." yace "Kwarai Hajiya, ai daga yau bazaki sake jin wata masala ba." ban kuma bi ta kan sa ba nawuce part É—in su Inna Wuro." A parlour na tadda su Bappa suna breakfast na zauna nima bayan mun gaisa Inna Wuro tazubo min kayan breakfast ta turo min gabana, nan nashiga ci muna É—an taÉ“a hira. Bappa yace "Mutanen sun tafi makaranta ko?." nace "Eh sun tafi." Bappa yayi murmushi tare da faÉ—in "Yanzu kam an bar kuka idan za'a tafi." "Dama ai rashin sabo ne yanzu kam an saba." cewar Inna wuro. Bappa yace "Hakane kam wai me yasa ne aka sauya musu makarantar ko yayi musu nisa ne? ko da yake *HAM'NAS* International School yafi shi nisa, me ya sane?." "Babu tsaro yan da yakama ta a makarantar shi yasa." nafaÉ—a a takaice. Inna wuro tace "Hakkum gaskiya sabo da Allah kam ya kamata su kara sa ido kan É—aliban su, susan duk wani wan da zai kawo É—alibai yakuma zo É—aukar su, duk da dai ranar Malam yace min mutumin kirkin nan ne Ahmad Tijjani Sabil yaje ya É—auko su ake tunanin ko masu garkuwa da mutane ne, amma dai ya dace sosai su sa ido kan É—aliban su." kai kawai na jinjina batare da nace komai ba,akasan raina kuwa faÉ—i nake "To waya sani ma ko mai satar mutanen ne dole zan sa jami'an tsaro cikin gidan nan tun da har ya fara shiga cikin gidan nan yana leken asiri." maganar Bappa dana ji shi ya kashe min zancen zucin danake "HAMDAH har yanzu banji kin ce komai ba kan maganar mu ta rannan, Yakamata yanzu kam kiyi aure ki fidda miji na gari kiyi aure, domin darajar ki yadaÉ—a ninkuwa, kwanakin can munyi maganar nan bakice komai ba, daraja da kimar hace baya É“ata cika cif har sai tana tare da abokin rayuwa wato mijin aure." tea É—in da na kurÉ“a ne nahaÉ—iye shi da kyar, sam bana son jin wannan kalmar gaba É—aya naji nakoshi da abincin a hankali na mai da cup É—in na aje kana a hankali nasoma magana. Bappa aure kuma, ai ni bazan yi aure ba rayuwa ta a haka tafi min." yace "A kul É—in ki kada na sake jin wannan maganar, a wannan shekarun naki zaki ce baza kiyi aure ba, nutsuwa bata taÉ“a cika sai da abokin rayuwa, kiyi na zari sosai ga abokan kasuwancin ki da suke zuwa gidan nan, ko wannan Alhj Muttari nan ai mutumin kirki ne ko ranar yaso yimin zan cen sai dai bai fito muraran yayi maganar ba, in yaso sai ku dai-dai ta kiyi auren ki kamalar ki ta daÉ—a cika." Inna Wuro tace "In ban da HAMDAH ma ai mutane basu taru sun zama É—aya ba, dan wani abu yafaru da rayuwar auren ki na fari bashi zai sa nan gaba yakuma faruwa ba,ai Allah baya taÉ“a jarabtar bawan sa da abun da bazai iya ba, duk kuma musulmi an sanshi da karÉ“ar kaddara me kyau ko mara kyau, ki gode masa ta hanyar kuma kara yin wa ni auren." "Hmm." kawai nace dan bana jin kamar abun da suke faÉ—an zai kasan ce, har can kasan kololuwar raina bana jin zan kuma aure, babu abun da natsana a yanzu kamar aure. meye acikin auren ban da tashin hankali da musifa, in dai har aure nutsuwa ce kamar yan da suka faÉ—a to gara na tabbata ni bani da wannan nutsuwar. Duk wani nasiha da jan hankalin da su Bappa suke jin su kawai nake,dan a yanzu babu abun da nafi tsana ma kamar aure!. sai da na bari suka gama yi min nasihar kafin na mike nace dasu zanje na É—an kwanta kafin su Naseem su dawo, abin cin da ban karasa ci ba kenan nafito. ina fita daga side É—in wata mota na shigo wa cikin gidan, a hankali na ke tafiya har na iso in da motar tayi parking kasan cewar dole sai nabi ta hanyar kafin na wuce side É—ina, ina isa dai-dai in da motar take sai ji nayi an.......! Mommyn Twins ce 8/19/22, 10:55 - Ummi Tandama😇: Da sauri cikin matukar tashin hankali tun kan ya karasa abun da zai faÉ—a na ce "Tamutu tamutu ko?!!." nayi maganar hankali a mugun tashe dan nagama tsinkewa da yan da naji yake maganar. ya ce "A'a Madam ba mutuwa tayi ba, dama bata da lafiya ne?, tun zuwan su School É—in Aunty'n su tace taga yanayin ta kamar batajin daÉ—i, shine ta tambaye ta sai tace mata wai kan ta keyi mata zafi, to tafita taje ta É—auko magani a office kenan ta dawo ta samu tana rike da kanta tana kuka tana faÉ—in kanta zafi, kan tayi aune ma ta faÉ—i kasa a sume, tun É—azu muna asibiti ban so kira na sanar ba sai ta farfaÉ—o amma har yanzu likitoci sun kasa shawo kan ta." "Innalillahiwa'inna'ilaihirraji'un wlh lafiyar ta lau ta bar gida." na furta da karfi yayin da jikina ke cirawa cikin azama na duro a gadon wayar na kare a kunnena ina tambayar sa wani asibiti ne, yana faÉ—a min nakashe wayar batare da na tsaya sauraran abun da yake cigaba da faÉ—a ba. wardrobe na buÉ—e na janyo mayafi na takalmi mara tudu na saka da sauri nafita na nufi Æ™asa, bibbiyu nake haÉ—a steps,ina sauka na nufi kofa har ina haÉ—awa da sassarfa. su Talatu suna zaune cukin parlour'n da sauri suka mike ganin yanda na sauko a firgice, tambaya ta me ke faruwa suka shiga yi suna biyo ni a baya, tuni nayi waje ban tsaya basu amsa ba, har parking lot suka bini, suna tambayar abun da ya faru. sai a lokacin na ce da su "Nasmah ce ke asibiti asume." salati suka shiga yi suna tambayar garin yaya. wan nan karon ban tsaya basu amsa ba dan ji nake tsayuwa basu amsa ma É“ata lokaci ne. kan kace me sabbin Security É—in da aka zuba cikin gidan sun iso in da muke, ganin yan da su Talatu suketa rafka salati, suma duk tambayar da suke ban tsaya basu amsa ba, su Talatu ne suka sanar musu abun da ke faruwa. Yakubu nashiga kwaÉ—awa kira, da sauri haÉ—e da gudu yafito daga cikin É—akin su, da sauri na shige cikin mota, yana ganin haka ya koma É—akin da sauri ya fito rike da makullin motar cikin hanzarin yashige motar. cikin matukar da muwa da rawar murya nace "Yakubu kayi sauri ko ka bani key É—in motar ni naja." key yayi wa motar tare da figar ta aguje, da gudu mai gadi ya buÉ—e get muka fita a gidan, sai da muka haura titi kafin yake tambaya ta in da zamu nafaÉ—a masa sunan asibitin. duk gudun da Yakubu yake gani nake kamar bayayi asibitin tayi min nisa. Number da aka kira ni da shi aka sanar min da tana asibitin na kuma kira wayar tayi ta ring ba'a É—aga ba, kuka ne naji ya zo min nayi saurin toshe baki na a raina nake faÉ—in "Shike nan ta mutu." kokarin mai da kiran nake dai-dai nan najiyo muryar Yakubu yana faÉ—in "Hajiya mun iso." da sauri na É—ago dan ban san har mun iso ba. da sauri na buÉ—e motar na fito batare da na jira faÉ—in da yake bari ya zo ya buÉ—e min motar ba. da sauri haÉ—e da sassarfa nayi cikin asibitin, a kofar shiga cikin parlour'n asibitin na haÉ—u da Aunty'n su Nasmah tana kokarin fitowa cikin sauri take tafiya da ka ganta gaba É—aya hankalin ta a tashe yake. tana gani na ta juya da sauri tana faÉ—in "Madam ta farfaÉ—o amma tana ta kuka." da sauri nabi bayan ta ina faÉ—in "Ina take." tun da ga cikin parlour'n nake jiyo kukan ta, da gudu nanufi kofar room É—in da nake jiyo kukan ta ciki, wasu daga cikin ma'aikata asibitin sukayi yunkurin dakatar da ni, ban ko saurare su ba na tura kofar na sa kai ciki. ina ji Yakubu daya biyo ni yana sanar musu da ko ni waye. Likitoci har guda uku a tsaye a kan ta suna rirrike da ita sai ihu take tana bige-bige, da gudu na isa in da take na kusa sakanin su na rungume ta,sai kawai nima na fashe da kuka ina faÉ—in "Nasmah me ya same ki, me ya same ki Nasmah?!!." kuka sosai na ke ina rungume da ita, itama kukan take tana ta fisge-fisgen nan kamar wacce bata cikin gayyacin ta. Turo kofar aka yi da karfi yana gaba wani na biye da shi. in da muke suka karaso da sauri, wan da ke biye da shi É—in ya dubi likitocin da ke cikin É—akin yana faÉ—in "Wai har yanzu bakuyi wani abu a kai ba?." cike da girmamawa sukace "Sir muna kai kenan yanzu ta farfaÉ—o so taki tsayuwa Muna kan kokari ke nan mu shawo kan matsalar, ruwa za'a saka mata sai dai taki tsayuwa sau uku ana samun jijiya sai ta gauce ya É“ata, zamu nima ta kafan ta ko kai ne a saka mata, na hannayen ta kam duka mun rasa su." cikin faÉ—a Dr da suka shigo tare da Ahmad da alama shine babban su ya ce "Shirmen banza sai kace ba ai kin ku ba." sai kuma ya dubi Ahmad ya ce "Sorry Sir ko mai zai dai-dai ta insha Allah." kai kawai Ahmad ya jinjina ya É—an maso in da nake rungume da ita ya ce "To meye amfanin kukan, kin rungume ta kina kuka ita tanayi, to da wanne zata ji da ciwon da ke damin ta ko da wannan kukan naki?." hannu ya mika ya É“amÉ“are ta a jikina, sake masa ita nayi dan na rasa abun yi guda É—aya ganin yanayin nata yakuma jefani cikin kiÉ—i ma, da firgici da tashin hankali, ya É—ago ta ya saka ta a kafaÉ—ar sa ya na faÉ—in "Kun É“ula ta da yawa dubi yan da hannayen ta suka fara kumbura." "Sorry Sir ta ki tsayuwa ne." É—aya daga cikin likitocin yafa É—a. tsaki yaja kana ya ce "Me yasa tun kan ta farfaÉ—o baku ni mi jijiyar ba, sai da ta farka zakuyi ta É“ula ta." "Sorri Sir hakan bazai yiwu ba do le sai ta farfaÉ—o." tsaki yakuma ya, yana jijjiga ta da bubbuga bayan ta, yana faÉ—in "Shiiit ya isa sorry baby yi hakuri kin ji sorry sorry." maganar yake daf kunnen ta yana ci gaba da jijjiga ta da bubbuga bayan ta. baya nayi, najin gida na da jikin garu-bango, ina mai cigaba da kukan cikin yin kasa da sauti. Dr da suka shigo da shi ya ya nufi kofa yana faÉ—in "I'm coming Sir." sai yayi waje sauran likitocin suka bi bayan sa. bai yi magana ba sai ci gaba da jijjiga ta da hura mata iskar bakin sa cikin kunne yake, a hankali kukan nata yarika raguwa, sai ajiyar zuciyar da take sauke wa a kai a kai, har tayi shiru tana mai cigaba da sauke ajiyar zuciya. jim kaÉ—an likitan ya dawo wannan karon su biyu suka shigo, yana gaba É—aya daga cikin waÉ—an da É—azu suke kan ta na biye da shi rike da wasu kayakin amfani irin na ma'aikatan lafiya. Dr ya dubi Ahmad da murmushi yana faÉ—in "Ikon Allah abun da mu likitoci muka kasa yi gashi uba yayi wa É—iyar sa, baby da ma so kike sai Daddy'n ki yazo kafin ki bamu damar yin ai kin mu ko." yayi maganar yana leko fuskar Nasmah da ke lumshe da alama bacci ke son É—aukar ta. murmushi Ahmad yayi yana shafa kanta, kana ya ce "Yan zu zaku iya yi mata abun da ya kamata." Dr ya ce "Okay." ya mika hannu ya karÉ“e ta yana kokarin kwantar da ita kan gado. ai ko ta buÉ—e ido tare da sakin kuka. da sauri Ahmad ya É—auke ta yashiga jijjiga yana faÉ—in "Shiiit Nasmah ya isa yi shiru jinki." ai ko tayi tsitt,har kuma lokacin ida nunta suna lumshe. zama yayi bakin gadon kana a hankali ya kwantar da ita yana É—an jijjiga ta da faÉ—in "Sorry kwanta a saka miki magani kiji sauki ko,babu zafi yanzu a gama miki mu tafi hawa doki." alama yayi wa Dr da ya soma ai kin sa, yakuma ce masa yabita a hankali, kana shi kuma yarika shafa kanta yana yi mata magana a hankali daf da kunnen ta. a hankali likitan ya soma gudanar da ai kin sa irin na kwararren likita. bugun fari ya samo jijiya a hannun ta na dama, batare da É“ata lokaci ba ya É—aura mata ruwa mai É—auke magunguna masu karfi da inganci. nan da nan cikin sakanni kalilan bacci yayi gaba da ita. bayan likitan yagama duk abun da ya kamata ya dubi Ahmad yana faÉ—in "Allah ya sawaka in sha Allah ko mai zaiyi normal idan ta farka." ya an sa da amin kana likitocin suka fita. Numfashi na sauke mai sauti san da ido na ya sauka kan Nasmah da ke bacci tana sauke numfashi a hankali, idanuna na rumtse tare da jan sheshsheka cikin kukan da nake har lokacin, sai dai zuwa yanzu kukan nawa a hankali yake fita. cikin zuciya ta nake yiwa Ubangiji godiya ganin ta sami bacci. har lokacin yana sunkuye a kanta yana shafa kanta yayin da É—aya hannun sa ke rike da hannun ta da akayi mata karin ruwa. maganar sa najiyo yasani buÉ—e idona a kan sa. "Ke kin ishe mu da wannan koke-koken na ki, kifita waje kije kiyi sa a can kin dame mu, ko so kike ki tashe ta da Wannan kukan naki mara amfani, tun tuni yarin ya tana tare da ciwo kin barta da shi a jikin ta har sai da yayi (C), ke baki da wayon sanin yaro bashi da lafiya ne, a hakan ne kike cewa ke zaki iyar musu yaushe kikayi wayon kula da kanki bare ki kula da su." baki na murguÉ—a cikin zubda Æ™walla na buÉ—i baki zanyi magana, sai wayata ta fara ring, dago wayar nayi ina mai share hawaye ganin Bappa ke kiran, sai nayi picking call É—in na kara wayar a kunne, daga cikin wayar Bappa ke faÉ—in "HAMDAH wani asibiti ne?." ina faÉ—a masa sunan asibitin ya kashe wayar. Zama nayi kan kujerar da ke gefe na jin kafata ta gaji sosai, ina mai ai ka masa da harara ina ci gaba da murguÉ—a masa baki. magana ya soma yi yayin da idanun sa ke kan Nasmah da take ta baccin. "Wayon ki a iya nan kaÉ—ai ya tsaya, sabo da ke baki da wayon magan ce naki shine ita ma zaki barta da shi ko, dubi idon ki ke kan ki ma baki da lafiya amma baki da wayon da zaki iya magan ce ciwon naki." a fusace cike da tsiwa nace "Idan kai ke raba wayon bana so karike shi, har abada kada nayi wayo." nayi maganar ne cike da jin haushi, ban san meye damuwar sa na jifana da kalmar rashin wayo a koda yaushe a duk san da muka haÉ—u da shi ba. yabi ya ishe ni da wasu maganganu ya barni naji da damuwar ciwon Æ´ata. fuskar Nasmah ya shafa tare da sakin murmushi har sai da dimple É—in fuskar sa ya bayyana. baki na taÉ“e tare da kawar da kaina gefe, dan zuwa yanzu hankali na yafara kwanciya, bai kuma magana ba sai zaman sa daya gyara ya daÉ—a gyara rukon hannun Nasmah da ke hannunsa sakama kon É—an zaburan da tayi cikin bacci. ni ma ido na na mai da kan waya ina É—an lallatsawa. Tun daga can waje nake jiyo muryar su Bappa ina kokarin mike wa suka turo kofar, Bappa na gaba Inna Wuro Faty Yakubu da Sule direban su Bappa, suka shigo. hankali tashe Bappa yake faÉ—in "Subhanalillahi garin yaya me ya same ta haka?." dai-dai nan suka karaso bakin gadon da Nasmah take kwance. Bappa ya leko fuskar ta yana cigaba da faÉ—in "Amma ta farfaÉ—o ko." Ahmad ya ce "Eh ta farfaÉ—o yan zu dai bacci take." "Masha Allah, kaji ikon Allah ko yarin ya tabar gida lafiya sai kuma ga ciwo, kai sannu Nasmah." Inna Wuro ta faÉ—a tana shafa kanta. Bappa ya dubi Ahmad yana faÉ—in "Sannu Ahmad sannu fa da kokari Allah ya saka da alheri." murmushi yayi kana suka shiga gaisawa, bayan gaisuwa da jajen abun da yafaru Bappa ke faÉ—in "Wai haka kawai ta suma kuma me likita ya ce ke da mun ta?." Ahmad da idanun sa ke kan Nasmah dake ta baccin ta har yanzu kana ya ce "Typhoid ne har yayi mata (C) da mamaki ace wai ciwo irin haka har yayi yawa a jikin yaro irin haka ba'a sani ba, har yakai matakin da zai iya sumar da ita wai duk ba'a sani ba." Bappa ya ce "Ikon Allah amma kuwa abun da mamaki, wai da ma bata da lafiya ne HAMDAH? ko irin zazzaÉ“i a tsatstsayen nan ne take?." ya karasa maganar yana duba na. da sauri ganin yan da wannan Ahmad É—in yake taso ya mai da alhakin ciwon ta kaina. na ce "Lafiyar ta lau bata kuma zazzaÉ“i a tsatstsaye." "Kuma bata taÉ“a ce miki wani gurin ta na ciwo ba, yaro ke nan Allah sarki kuma kema baki taÉ“a lura da yanayin ta ya sauya ba." cewar Inna Wuro, tayi maganar cikin jimami da alhinin ciwon nata. "Babu wani alamar da na taÉ“a gani na ciwo tattare da ita, kuma bata taÉ“a cemin wani gurin ta na ciwo ba, in ban da shekaran jiya da nake kwance kai na na ciwo ita ma tazo ta ce min kanta na mata zafi, kuma nasan a lokacin É—in dan nima na ce kai na nayi min ciwo ne shi yasa ita ma ta faÉ—a." nakarasa maganar ina É—aga hanci sama dan ganin yan da É—an shishshigin nan keta wani girgiza kai. da sauri na mai da idanuna kan sa jin yana faÉ—in "Ashe dai ta ma faÉ—a miki bata da lafiya amma bakiyi serious a kai ba, dan ta faÉ—i kan ta na zafi lokacin da naki yake ciwo sai ya zama nata karya ne?, taya za'ayi ki fahimci hakan tun da baki da wayon sanin haka." ido na waro baki buÉ—e jin yakuma jifata da kalmar rashin wayo,wai shin wannan mutumin me yake jin kansa ne,shi ji yake yafi kowa wayo kowa yi masa kallon rashin wayo yake?. a kufule na buÉ—i baki zanyi magana, Bappa ya katse ni da faÉ—in "Ai shi yaro idan ba lura kayi da yananin saba wani É—an bashi da azancin faÉ—ar abun da ke damin sa, ko da yana jin wani gurin sa na ciwo, sai dai in kai ka gane hakan daga yanayin sa na yau da kullum, kirika lura da yanayin su tanan zaki rika fahimtar ciwon su, Allah sarki da gaske kan nata nayi mata ciwon ne sai tace yana yi mata zafi, Allah yabaki lafiya Nasmah." Amin duk aka amsa da shi, baki na tura gaba muna gaÉ—a ido dashi na murguÉ—a masa baki, wani murmushi ya sake sai da dimple É—in sa suka bayyana,ya mai da idanunsa kan Nasmah yayin da fuskarsa ke nan É—auke da murmushin nan. ido na É—an kurawa fuskar sa wan da dimple ya daÉ—a kawata shi. baki na taÉ“e ina mai É—auke idanuna a kansa... Muna nan cikin É—akin kiran sallar azahar ne yasa su Bappa fita dan zuwa masallaci, har da shi, yarage daga ni sai Inna Wuro da Faty. Inna Wuro ta shiga toilet É—in cikin É—akin ta yi al'wala tafito tace da ni naje nima nayi muje masallacin cikin asibitin muyi sallah, tun da ga Faty in muka dawo sai itama taje tayi... muna isa masallacin ana idar da sallah, su mazan suka koma ciki mukuma muka shige cikin masallacin. ko da muka idar muka koma ciki, abakin gadon na kusa da Nasmah in da É—azu yake nan yanzu ma yake zaune. zaman mu baifi da minti 20 ba akayi knocking É—in kofa, Yakubu dake tsaye ta kusa da kofar yabuÉ—e. wasu maza guda biyu suka shigo niki-niki da kayan abinci duk kanin su sanye da rigonan irin na ma'aikatar hotel. cikin girmamawa suka shiga gaida Ahmad kana suka gaida Æ´an cikin É—akin, suka dire manyan basket É—in dasuka shigo dashi, nan suka shiga zuba abinci suna mikawa kowa, da mamaki nake kallon su dan nidai a sani na ban bada umurnin kawo abinci daga wani hotel ba. maganar É—aya daga cikin mutanen naji ya na faÉ—in "Gashi hajiya." É—ago idanuna nayi daga kan wayar da nake natsawa na dube shi, plt É—in abinci yake miko min, kai na girgiza tare da faÉ—in "Nakoshi." "A'a me kikaci HAMDAH nasan tun fitar ki ba abin da kika ci." cewar Bappa yana duba na. "Bana jin yunwa." nafaÉ—a ina mai da idanuna kan wayar. "Zama da yunwa bashi da amfani wan da gashi komai yazo da sauki kici abinci itama bakiga tana baccin ta ba, sauki ce ke samuwa cikin bacci insha Allah." Inna Wuro ta ce "Insha Allahu kuwa lafiya nata kan samuwa." ni dai ban kuma cewa komai ba, plt É—in abincin suka mikawa Faty dake kusa da ni. wani É—an ma dai-dai cin basket daga cikin waÉ—an da suka shigo da su, abincin cikin sa na musamman shi suka zuba masa suka mika masa hannu ya daga tare da faÉ—in "Akarawa kowa yaci." Bappa da yakai loman abinci yahaÉ—i ye ya ce "A'a Ahmad ai wannan ma ya ishe mu maza karÉ“i ka ci wannan ya ishe mu haka ga abibci nan idan bamu koshi ba duk zamu kara, Allah ya saka da alkhairi an gode sosai Allah yakara buÉ—i." Jin yan da Bappa yake ta zuba masa godiya yasa nasan cewa shi yayi odar abincin, baki na taÉ“e a raina nake faÉ—in "Sai kace ance masa bamu ci abinci bane ko yunwa ke damin mu." wayar sa ce tayi kara yamike yafita batare da ya karÉ“i abincin ba, Bayan sa nabi da kallo "Gulma shi da yasa a kawo dan tsabar gulma shi ne yaki ci to da waya mai da mayunwata." Faty dake daf da ni ta juyo tare da faÉ—in "Adda HAMDAH me kika ce?." "A'a bada ke nake ba da wancan É—an gulmar nake." "Wafa?." ta faÉ—a tana kallon waÉ—an da suke cikin É—akin. "Ba kowa." na faÉ—a ina mai da idanuna kan waya. tun da ya fita bai dawo ba ganin ya jima sosai bai dawon ba yasa nayi tunanin ya tafi ne, gara ma ya tafin É—an shishshigi. har wajen la'asar muna nan zaune Nasmah bata farka ba zuwa lokacin kam bakin gadon na dawo na zauna. akai-akai likitoci ke zuwa duba ta, tun bayan fitar sa. ana kiran sallar la'asar su Bappa suka fita bayi Inna Wuro ta shiga ta É—auro al'wala tafito ta shinfiÉ—a sallayar da nasa Yakubu ya É—auko a mota, ina nan zaune kusa da Nasmah da har lokacin take ta kan bacci, ido na tsura mata gaba É—aya yanzu na kagu ta farka. na É—au alwashin duk likitan da yakuma zuwa zai saka wani allura cikin drip É—in dake shigan ta zan hana, dan na lura kamar shi ke da É—a sata cigaba da baccin. ban tashi ba har sai da Faty ta idar da nata sallar, kana nashiga toilet É—in room É—in bayan nayi al'wala nazo na gabatar da salla. ko da na idar ina nan zaune kan sallayar ina lazumi,da sauri na É—ago kaina jin Inna Wuro tana faÉ—in "Nasmah kin farka ne?." da sauri na mike ganin tana É—an motsa hannun ta, da sauri Inna Wuro dake gefen ta ta roko hannun nata da aka mata karin ruwa da shi take ta kokarin É—aga shi, cikin hanzarin na iso bakin gadon ina faÉ—in "Nasmah Nasmah tashi kada ki sake komawa baccin nan." a hankali ta buÉ—e idanun ta na bin cikin É—akin da kallo. sannu Inna Wuro da Faty suka shiga jera mata. É—aya hannun ta na roko da murmushi ganin idanun ta wasai naci gaba da faÉ—in "Sannu Nasmah kan naki ya dai na yi miki zafin?." fuska ta kwaÉ“e sai kuma ta fashe da kuka. "Subhanallahi yi hakuri kinji Nasmah yi shiru kinji idan kikayi kuka kan zai ci gaba da yi miki zafin fa yi shiru abin ki." Inna Wuro ta faÉ—a da alamun rarrashi. kai na gyaÉ—a tare da faÉ—in "Eh kin ji yi shiru abin ki Nasmah." sautin kukan nata takuma karawa tana ta kokarin fizge kannulan da ke hannun. da sauri ya turo kofar ya shigo , cikin hanzari ya iso bakin gadon. ta gefen da nake ya tsaya tare da ruko hannun ta da hannuna ke kai, da sauri na É—auke hannuna dan yan da ya sauke hannu nasa kan nata sai da ya taÉ“a nawa hannun. É—an matsawa nayi ganin yan da mukayi daf da juna. "Shiiit ya isa haka bar kukan nan." ya faÉ—a yana shafa kanta kana ya É—ago wayar sa ya daddanna ya kai kunnen sa "Na shigo." yayi maganar yana sauke wayar. kan ta yaci gaba da shafawa yana kuma cigaba da faÉ—in "Yi shiru bari azo a cire miki wannan abun ki huta." Cikin mintinan da basufi 3 zuwa 5 ba Dr ya shigo ya cire mata ruwan dan dama saura kaÉ—an ne ya rage, a na cire mata Ahmad ya É—ago ta ya saka ta kafaÉ—ar sa yashiga jijjiga ta har tayi shiru. bakin gadon ya zauna kana ya É—aura ta kan cinyar sa, ya dubi Faty ya ce "Fatimah haÉ—a mata tea ta sha." yayi maganar yana kallon basket É—in da ma'aikatan hotel É—in nan suka zo da shi suka tafi suka barshi a nan cikin room É—in. Faty ta ce tom. ta haÉ—o tea É—in da sauri ta mika masa, ya amsa, tare da gyara wa Nasmah zama kan kafarsa ya saka mata cup É—in a baki yana faÉ—in "Sha maza muje ki hau lilon doki daga gun kisha Chocolate ko." ai ko tabuÉ—e baki ya kafa mata cup É—in, sai da tasha fin rabi kafin ta É—aga kanta. Dr dake tsaye a gefen su yayi dariya tare da faÉ—in "Nasmah Daddy ne kaÉ—ai mai yin rarrashi a yarda ko?." Inna Wuro ta ce "Ai kam mu duk rarrashin da zamuyi sai dai ta sa mana ihu." duk sukayi dariya ban da ni da kuma shi da ya murmusa. "ÆŠan shishshigi." nayi maganar a kasan raina tare da jan guntun tsaki a fili. duk suka juyo suka kalle ni. Inna Wuro taciga da faÉ—in "Har uwar tata ma taki yar da rarrashin nata." mike wa yayi tare da sakata a kafaÉ—ar sa yasoma tafiya tare da faÉ—in "Tasan itama bata wuce rarrashin bane." yana kaiwa nan yayi waje Dr ya rufa masa baya, ido na waro tare da yin kwafa wannan mutumin sainayi maganin sa. Inna Wuro da Faty kuwa dariya sukayi. Faty ta É—auki sallayar da mukayi sallah muka nufi waje. a can farfajiyar asibitin muka iske su suna tsaye suna magana da Bappa. kafin mu karaso ya shige motar sa in da ya saka Nasmah a gefen sa yaja motar mai gadin asibitin ya buÉ—e masa get ya fita. cikin takaici haÉ—e da mamakin karfin hali irin nasa nabi bayan motar da kallo. bansan dalilin sa na son yimin shishshigi cikin rayuwa ta ba, akan wani dalilin zai tafi da ita, to ma ina zai kaita tun. maganar Bappa naji yana faÉ—in "HAMDAH muje ko." juyowa nayi sai gani nayi har kowa ya shige mota. "Bappa akan wani dalili zai tafi da ita?." ya ce "Gida zai kai ta dan taki yar da na karÉ“e ta kuma aciki ma yace min taki yarda da ku,idan ya barta zatayi ta kuka ne kuma likita ya ce ba'a so tarika kuka, sabo da ciwon kannan nata sai ya iya motsa mata, muje zamu same su a gida ma yan zu, yaron arziki mai son taimakon al'umma." da sauri na ce "Waya ce masa bukatar taimako muke." nayi maganar ina waigin hanyar da suka fita tare da murguÉ—a baki kamar yana gani na. murmushi Bappa yayi kana ya ce "Babu wan da ya ce masa ana bukatar taimako halinsa ne hakan." juyawa nayi na shige cikin mota ba tare da na kuma cewa komai. Koda muka isa gida ganin babu motar sa yasa nayi tunanin ko har ya ajiye ta ya wuce ne, da sauri nashiga ciki. Naseem da ke tare da su Zulai ya rungume ni yana yi min oyoyo. su Talatu sunayi min sannu da dawowa ya mai jiki, ban iya basu amsa ba sai tambayar su nayi "Ina Nasmah?." "Hajiya ba tana asibiti ba." cewar Zulai. kaina girgiza tare da faÉ—in "An dawo da ita gida." Talatu tace "A'a Hajiya ba'a dawo da ita ba." da sauri na juya nafita waje a sakar gida na tadda su Bappa suna kokarin wucewa part É—in su na ce "Bappa bai fa dawo da ita ba." murmushi yayi tare da faÉ—in "Zai dawo da ita je ki huta." juyawa kawai nayi badun naso ba sai dun bana so nayi masa musu. Nakai tsawon awa guda zaune cikin parlour zaman jiran dawowar ta, ganin guri ya fara rufawa magriba ta kusa sai na mike na haura sama, sai da nayi wanka na gabatar da sallar magriba kafin na sauko. nasa Zulai ta kawo min tea sai a lokacin na sa wani abu a ciki na. zuwa yanzu kam ina ji bazan iya cigaba da hakuri da sa sammanin dawo da ita ba, yunkurin mike wa nayi dan zuwa gurin Bappa, ya faÉ—a min gidan sa naje na É—auko Æ´ata. da sauri na waigo kofa jin an turo kofar parlour'n........! Mommyn Twins ce 8/19/22, 10:55 - Ummi Tandama😇: Tun da yatafi masallaci bai shigo gidan ba sai bayan sallar isha, dan tun san da aka idar da sallar zai koma ciki, yayi ba'i dan haka yasa akayi musu masauki a parlour'n ba'i, basu kuma bar gidan ba sai daf magriba, dan haka masallaci ya zarce sai yanzu bayan sallar isha ya shigo. ko da yashigo parlour'n babu kowa, sai sanyi me fidda daddaÉ—an kamshi ke tashi cikin parlour'n. direct bedroom É—in sa ya wuce, hular kansa ya cire ya É—aura saman bedside, kana yatafi a hankali zuwa bakin gado ya zauna, a hankali yakai bayan sa ga katifa ya kwanta rigingine, yayi pillow da hannayen sa kafar sa na kasa yana É—an lilo da shi. shiru yayi yayin da ya kurawa pop'n É—akin ido, kamar mai karantar wani abu a jiki. a hankali ta turo kofar ta shigo da sallama, ido ta kura masa na Æ´an dakikai kana a sannu ta taka zuwa bakin gadon, sai ta faÉ—a jikin sa gaba É—aya ta sake nauyin ta a kansa, ido ya waro tare da faÉ—in "Wash zata karya ni, Kawa kin kara nauyi fa." cikin muryar dariya ta ce "Allah Aboki babu wani nauyin dana Æ™ara in da nake da haka nake yanzu ma." "Tap waya faÉ—a miki ke baki ganki kwana biyu sai daÉ—a zama duma-duma kike ba, niko sai tatse ni kike." kwanciyar ta tadaÉ—a gyara wa a kansa cike da shauki tace "Kai Aboki kai ma fa baka ganka bane kayi kiba kwana biyun nan." dariya yayi yana dai-dai ta fuskar su a hankali ya manna mata kiss kan laɓɓanta. yan da suke yiwa junan su idan ka gani zaka fagimci santsar kauna soyayya shakuwa yarda a saka nin su. cike da shauki ya mirgino ta yadawo da ita kasa shi ya haye kanta, nauyin sa shima ya sake mata, yana faÉ—in "A hakan kike cewa nayi kiba jini fa babu ko nauyi kamar pepa kullum kina tsotse ni, kullum sai na tsame wani abu daga jikina na zuba shi jikin ki, taya bazaki daÉ—a kara zama wata duma-duma ba." Æ´ar karamar kara ta sake tana faÉ—in "Allah Aboki kayi nauyi wash Aboki na tuba É—aga ni." Æ´ar dariya yayi tare da shafa sumar kanta yana nan a kanta. Æ´an wasan ni suka cigaba da yi sakanin su me cike da zallar shauki da kauna, zallar soyayya da É—in bin kauna kake hangowa tsagwaran ta a tattare da su. Cikin yanayin da suke ta dube shi tana faÉ—in "Aboki ka rama É—aga ni na tashi, idan ka kara yafi haka nima sai na rama." tayi maganar tana ture shi. Æ´ar dariya yayi mata tare da mirginawa ya koma gefe yakwanta rigingine tare da yin pillow da hannayen sa biyu, ta mirgina tayi pillow da damtsen hannun sa, sai kuma ta É—ago tasaka hannun ta a kumatun ta, yazamana da guiwar hannun nata najikin katafi, in da da kyau take iya kallon fuskar sa, duban sa tayi da kyau naÆ´an sakanni kana a hankali taso ma magana "Meke da mun ka aboki?." tayi maganar idanunta cikin nashi. idanun sa ya lumshe tare da buÉ—e wa yaÉ—an ja numfashi kana yace. "Tambayar É—azu kuma har lau, to me kika gani yanzu bacci nake ji." murmushi tayi kana ta shafa gefen fuskar sa sannan ta ce "Bacci kuma him Aboki kenan, adalilin yin baccin ka na rana zaka kuma yin wani baccin ne da misalin karfe 12 na dare, yanzu karfe 8:30 saura akwa uku da rabi lokacin baccin ka yayi, sam karya baya yi maka kyau sabo da rashin iya shi da bakayi ba shi yasa ko kayi ake saurin gane ka." kokarin kawar da maganar yayi ta hanyar janyo ta jikin sa, kana ya shiga wasa da wasu sassan jikin ta, a hankali ya furta "Kawa ke baki ga in da idona sukayi ba bacci ne a cikin su, da alama dai baccin da É—azu kika sani bai ishe ni ba." ta ce "Him wai ni yau ake É“oyin wani abun, Aboki yaushe ka fara É“oye min damuwar ka, yaushe ka fara sanya hijabi sakanin sirri na da naka, duk faÉ—in da kake ni da kai abu guda ne ashe ba haka bane??, shin da ma ashe akwai wata ranar da zaka É“oye min damuwar ka, ni ce fa wacce muke tauna matsalolin mu mu magance sa batare da wani ya sani ba, ashe dama faÉ—in mu tsirrin junan mu ne da kake abun ba haka yake ba, ban taÉ“a tunanin zuwan wannan ranar ba." É—an sakai ta maganar nata tayi tare da mike wa zaune ta tankwashe kafafun ta takuma duban sa da kyau, nan take sai ga hawaye yacika idon ta, hannun sa ta ruko ta kankame shi cikin nata, ta ce "Tabbas akwai abun da yake damun ka da ma ai ni na sani akwai ranar da zatazo irin haka." hannun sa ta daÉ—a kankamewa cikin nata, taci gaba da faÉ—in "Kayi hakuri amma ka sani nafika jin damuwa fiye da kai, ni na riga da nasa ni, dama kana hana ni damuwar ne kai kana yi, idan da a ce mutum shi yake ba kan sa abu da karfin dukiya WALLAHI dana sadaukar da dukiya, WALLAHI idan dana san in da zanje na sami maganin da zansha yazamo silar haihuwa dana tafi ko da bangon duniya ce,domin samin farin cikin ka, nagaza baka É—a kayi hakuri kayi hakuri kayi hakuri!!." takuma nanata kalmar hakuri yayin da tuni hawayen idon ta suka fara zuba. Da sauri yamike zaune tare da janyo ta jikin sa yana faÉ—in "Ke meya kawo wannan maganar?, banace kada nasake jin wannan maganar a bakin ki ba?,meye na yin ta meya kawo ta yanzu kuma?, Okay so kike ki kawar da farin cikin da ke nan ko?, hauhuwa dama ashe mutum shi yake bawa kansa haihuwa?, okay kin mance cewa Allah shi yake bai wa bayin sa haihuwa?, so kike kiyi tsaÉ“o to kiyi gaggawan tuba, maza yanzu." yayi maganar yana share mata hawaye. kana yaci gaba da faÉ—in "Dai na kunan kada na sake jin wannan maganar a bakin ki, kada na sake ji idan kuma so kike ki koyi yan da zaki rika É“ata min rai to ki kara yin ta, na ce miki ina son haihuwa Allah bai nufa na samu bane, idan yaso sai ya bamu bare ma muna da su Æ´aÆ´an da muke yi musu hidima kama daga gidan marayu makarantu da dai sauran su suÉ—in ba namu bane, suma Æ´aÆ´an mu ne, mai da hawayen kinji Fara Æ´ar duma-duma ta." " kai ta shiga girgiza wa tana faÉ—in "Nayi shiru bazan sake ba ka yafe min." kai ya jinjina kana ya koma yajin gina bayan sa da jikin gado, ita ko zaman ta tagyara suna fuskantar juna ya ce "Ko ke fa fara Æ´ar duma-duma ta to na yafe." dariya tayi kana taÉ—an langwaÉ“ar da kanta cikin muryar shagwaÉ“a a hankali ta ce "Na yar da ba abun da na faÉ—a yanzu ke damin ka ba amma na tabbata akwai wani abun, zuciya ta baza ta sami sukuni ba har idan ban za mo silar kawar da damuwar ka ba, amma babu damuwa tun da ka nuna baka so na sani, yau rana ta farko daka taÉ“a É“oye min damuwar ka, ban taÉ“a tunanin akwai ranar da zata zo ka É“oye min damuwar ka ba, damuwar ka tawa ce kamar yan da yake tawa takace, ai ban san cewa haka yanzu ka É—auke ni ba shike nan babu damuwa." tayi maganar tana kokarin sauka a gadon. dakatar da ita yayi ta hanyar rike hannun ta kana yaÉ—an ja numfashi sannan ya ce "Abar shi kawai faÉ—ar shi ma bashi da wani amfani." ido ta kura masa sannan tace "Haka kace abar shi yaci gaba da damun ka da cin ka a rai ko?, kada ka mance nafi kowa sanin ko kai waye tun sati biyu da suka wuce na fara fahimtar akwai wani abun da ke damun ka, ban daÉ—a gaskata hakan ba sai yau da ka shigo gida, rungumar ka da nayi jikin ka da zuciyar ka suka tabbatar min da haka, dakuma tabbacin damuwar naka yakaru a yau, tanbayar ka danayi É—azu da zaka tafi masallaci yakuma bani amsar abun da nake zargi, babu halin da zaka shiga koda dai-dai na second 1 ne ban gane shiba." Ganin yan da ta hakikan ce tanuna damuwar ta matuka a kanshi takuma nuna É“acin ranta nakin faÉ—a mata da yayi wan da ada ba haka asakanin su. sai ya janyo ta jikin sa ya rungume, tabbas ita wata sashi ce a rayuwar sa da bazai iya É“oye mata komai na rayuwar sa ba, kamar yan da tun fari suka gina rayuwar su ta hanyar faÉ—awa junan su sirrukan su, bata É“oye masa komai kamar yan da shima baya É“oye mata, ko a yanzu dayake ta kokarin barin abun cikin zuciyarsa shi kaÉ—ai yana ta shan fama da É—awai niya da zuciyar sa dan bai saba ba sam. numfashi ya ja kana a hankali yasoma magana "Akwai wani abun da ke damu na amma sam banso na fitar ba naso nayi jarumtar iya barin sa a raina dan faÉ—ar sa sam bashi da amfani." wani numfashi yakuma saukewa kana a hankali ya cigaba da magana "Kiyi hakuri da abun da naketa É“oye shi a zuciya ta ni kaÉ—ai, wan da nagaza iya dan neshi sabo da ban saba da irin saba, yabani wuya sosai a zuciya ta, kiyi hakuri yanzu da zakiji shi a kan laɓɓana, tabbas da gaske bazan iya É“oye miki sirri na ba kokarin yin haka dana yi kuwa dan cigaba da ganin kwanciyar hankalin ki yabani wuya sosai a zuciya, nayi ta kokarin danni shi cikin zuciya ta hakan ya garara gashi bugun farko kin gano da akwai abun da yake dami na." hannun ta ya damke cikin nasa kana yaja numfashi ya sauke sannan yaci gaba da faÉ—in "Wata ranar da Company na ya tura kayan bukata izuwa wata makarantar yara, kamar da yan da kika sani a ka saba, lokacin da motar Company ya isa aka shai da min da isar sa, sai na tashi da kai na naje makarantar domin ganewa ido na kalar farin cikin da yara zasuyi kan kayan da aka kai musu wan da yawan ci kayakin wasa ne irin na yara,sai sabbin kujeru, dan nima naji daÉ—i, duk da kuwa makarantar bana Gwamnati bane, makaranta ne ma irin na Æ´aÆ´an masu kuÉ—i, lokacin da na shiga makarantar nayi arba da wasu yara guda biyu, sunata wasanni da kayakin wasan da aka kai musu, duk da yara dayawa agurin amma nafi ganin farin cikin waÉ—an nan yara guda biyun sosai cikin matukar farin ciki da kuma jin daÉ—i suke ta wasa da kayan da motar Company na ta sauke, naji daÉ—i matuka ganin farin ciki a fuska da zukatan É—aliban, amma sai dai hankali na yafi karkata kan farin cikin da ke baiyana ga waÉ—an nan yara guda biyu, kasan cewar lokacin tashi yayi nan É—alibai suka fara watsewa, wasu diraibobin su suka zo suka kwashe su wasu kuma motar makaranta ta kaisu, haka yara sukayi ta watsewa. ina nan a cikin makarantar muna magana da shugaban makarantar bayan mun gama maganar na fito, lokacin tuni students sun watse, a bakin get na tadda waÉ—an nan yara guda biyun, da lokacin da na shigo makarantar su na fara ganin su da É—in bin farin ciki kan fuskokinsu, tare da mai gadin makarantar suna zaune a bakin get. ko da na iso gurin su kan su na shafa tare da duban mai ganin na ce, yaya su ba'a zo É—aukar su bane kokuma motar makaranta zasu bi kuma naga É—alibai duk sun watse. mai gadin ya ce Ba motar makaranta zasubi ba direban su ne zai zo ya É—auke su ko mai akayi dai yanzu yana hanya, yau an É—an makara ne wajen zuwa É—au kar su. kan su na daÉ—a shafawa sai nayi waje cike da jin sha'awar yaran, ina fita kuwa sai suka biyo ni a baya, sai na tsaya naruko hannun su ina tanbayar su yaya sunan su, kai yaya sunan ka nafara tambayar na mijin sai yace min sunan sa Naseem, ita kuma macen tace min sunan ta Nasmah, nafahimci wayo sosai tattare da yaran duk da kuwa Æ™arancin shekarun su, dan bazasu wuce shekaru uku zuwa uku da rabi ba, bayan nayi musu tambayar sai suma suka mai da min tambayar. to kai ma yaya sunan ka, wayon yaran ya burge ni sosai jin yan da suma suka iya mai da min tambayar, Sai nace musu sunana Daddy, kin san wani irin yanayi nagani a tare da su lokacin da nace musu suna na Daddy?." Dan sakai ta maganar yayi tare da daÉ—a matse hannun ta cikin nasa kana yaci gaba da faÉ—in "Ihun murna suka sake haÉ—e da tsalle suka rungume ni suna faÉ—in laa kai Daddy ne irin Daddy'n su Aeeman,É—in class É—in mu, to kai Daddy'n su waye ne?, maganar yaran yasa Ni shiga wani yanayi, sai dai farin cikin danake hango wa tare da su da kuma fahimtar da nayi kalmar sunan Daddy dana furta musu yazo mu su a sabon abu ko makamancin haka, Sai na ce musu Daddy'n ku. kin san me yaran sukayi?." nan ma hannun ta yakuma damke wa cikin nashi kana yaci gaba da faÉ—in. "Da É—a rungume ni sukayi suna ta tsallen murna da nanata kalmar sunan Daddy, wani irin abu naji acikin jiki na da zuciya ta, a duk san da suka furta kalmar Daddy a gare ni, sai naji wani irin farin ciki da jin daÉ—i mara misaltuwa a gare ni, cikin kan kanin lokaci naji yaran sun shige cikin zuciya ta, har nake ji tamkar Æ´aÆ´an da na haifa ne a gaba na suke kira na da wannan suna, abun da na daÉ—a lura da yaran a lokacin sosai na ke hango jin daÉ—i irin na samun sabon abu a tare da mutum, sai suka ce min Daddy kai ma zaka bamu chocolate irin wan da Daddy'n Aeeman yake bashi. na ce musu kwarai kuwa, to lokacin akwai ragowar Chocolate a mota wan da nake baiwa yara a gidan marayu idan naje, sai na ruko hannun su nace muje na basu chocolate yana mota ma kuwa. lokacin da muka nufi gun mota, a dai-dai lokacin wata yarin ya ta iso gurin a cikin mota." Sai kuma yayi shiru batare da yaci gaba da Maganar ba. ita ko zaman ta tagyara sosai wannan karon ita ta mai da tafin hannun sa cikin nata tasar kafe yatsun su guri guda, kana ta sanya idanun ta cikin nashi, cikin daÉ—a karfafa shi da bashi kwarin guiwar gama fidda damuwar da take ganin tamkar ta yaye masa, tagyaÉ—a masa kai cike da bashi kwarin guiwar yaci gaba da da fidda damuwar da take yi masa kallon cuta ce barin sa a ransa. A hankali kuwa yaci gaba da maganar yayin da ya daÉ—a sarkafe hannun nasu sosai, ya ce "Kawa kin san me naji?, wani abun mamaki naji wan da ban san mene ne shi ba, bayan da yarin yar ta É—auke su ta tafi da su, sai na tsinci kai na cikin wani irin yanayi mai ka ma da da muwa, mai kama da son in sake ganin su, amma nafi alakanta son in sake ganin yaran ne, bayan kwana biyu sai naji tunanin nawa yanata rikiÉ—a, madadin tunanin yaran su biyu sai ya dawo uku, zuwa lokacin na gama fihimtar har da ita yarin yar nake son sake gani. nayi mamakin kai na matuka, wata rana dana fita muka kuma haÉ—uwa da su a kan hanya ta ta zuwa mittin, a tunani na ganin da nayi musu wannan rana shike nan zuciya ta zata huta da tunanin abun da bai shafe ta ba, amma ina bayan rabuwar mu da su sai naji tamkar kara min ake. Bayan wasu kwana biyun sai nasa ayi min bincike a kan su wato ita da yaran dana ke yi musu kallon kannen ta ne, nayi mamaki matuka lokacin da labarin su ya iso min, dajin waÉ—an nan yara nata ne ma ana ita ta haife su. mamaki na shi ne ganin ta kara ma sosai, nasamu cikakken labarin su, da duk kanin bayanan tarihin rayuwar su..." shiru yayi tare da jan numfashi ya sauke, sannan ya ce "Labarin su mai cike da ban tausayi na girgiza da jin lamarin, sai dai a yanzu su ba abin tausayi bane, dan Ubangiji ya zartar da ikon sa gare su..." A hankali yashiga bata labarin su kamar yan da aka kawo mishi cikakken tarihin su, bai É“oye ko rage mata komai ba kamar yadda baiyi da farko ba, bayan gama shaida masa abin da aka sanar masa a kan su sai ya cigaba da faÉ—in "Kin san wace ce wannan yarin yar?." kai ta girgiza jiki a sanyaye yayin da idanun ta suka cika da Æ™walla tap suna shirin zubowa. taji bala in tausayin su da jin labarin su jikin ta yayi matukar sanyi. ya ce "I ta ce mai Company *HAM'NAS*." ido ta waro ta ce "Mai Company *HAM'NAS* mai *HAM'NAS* Nigeria Limited?." "Kwarai kuwa ita ce." kai ta jinjina tare da faÉ—in "Allah mai iko wan nan shine sakayyar da mafificin rahama yayi mata sakamakon cin jarabawar da ya É—aura mata tabbas labarin rayuwar ta abun a tausaya ne, a da yanzu kam Allah yayi mata sauyi da mafificin rahamar sa." sai gata tana hawaye cikin matsanancin tausayin labarin rayuwar HAMDAH da taji, har da jan sheshshe ka. ta kai hannun ta share hawayen ta tare da faÉ—in "Allah kayi mana mai kyau kasa mu dace duniya da kiyama." ya ce "Amin." sai ya saki hannun ta yakoma ya kwamta tare da lumshe idanun sa. a sannu ta gyara ita ma sai ta kwanta gefen sa tare da yin pillow da damtsen hannun sa, a hankali takai hannun ta kan fuskar sa, a sannu tashiga shafa gefen fuskar sa, in da kayataccen saje ke kwance a gurin lub-lub gwanin ban sha'awa. duban sa tayi da kyau cikin kulawa a hankali ta ce "Aboki." idanun sa da suke lumshe yaÉ—an buÉ—e su a kanta sannan ya amsa da "Na'am." in da ya am sa can cikin kasan mako shin sa, laɓɓan sa ne suka motsa tanan ta fahinci ya amsa kiran nata. idanun ta cikin nashi, sannan tace "Aboki bayan sanin labarin ta kuma sai me baka karasa bani labarin ba." idanun sa ya lumshi cikin son kawar da zancen ya ce "Wani labarin kuma ai na gama baki labarin." murmushi tayi tare da faÉ—in "Baka kara sa ba da saura dan acikin duk kanin labarin da ka bani baka bani asalin gundarin labarin ba, kawai dai ka ce min kana jin wani abu a kanta mene ne shi?." "Ba ko mai fa." yafaÉ—a a takaice yana gyara kwanciyar sa, tare da juya wa ya fuskanci jikin garu, yana faÉ—in "Zanyi bacci ki tai maka min kisa yayi daÉ—i." hannun ta ta cusa karkashin gashin kansa ta bayan keyar sa, yana jin haka da sauri ya juyo dan yasan jan masa sumar zatayi da karfi bawai tayi masa yan da zaiyi baccin ba. dariya tayi tana faÉ—in "Ai da baka juyo ba Aboki yau aski zan maka." ido yaÉ—an waro ya ce "Aski da hannu." farr tayi da ido ta ce "Zan nimo abin yin askin ai taÉ“awa nake naji ta in da zan fara." ya ce "FaÉ—i gaskiya dai Æ´ar guntun muguntar ce ta motsa." dariya takuma in da shi kuma ya murmusa yana kokarin mai da idanun sa ya lumshi tayi saurin dakatar da shi ta hanyar faÉ—in "Me zaka É“oye min ne iye sai fa ka karasa bani labarin nan dan baka gama bani ba." shiru yayi bai ce komai ba, Murmushi tayi tare da faÉ—in "To ni bazan karasa baka labarin, tun da yau ka aro hijabi ka sakata sakanin mu, zan yaye ta yanzu dan babu ita sakanin mu har gaba da abadan." É—an numfashi ta ja tare da cigaba da faÉ—in "Tun da ka sanya ido kanta Ubangiji yayi ikon sa,ya datsa maka sonta, a lokacin da baka taÉ“a sammanin a kwai ranar da hakan zata kasan ce da kai ba, dan kai a tunanin ka ni kaÉ—ai ce Ubangiji ya dasa maka sona cikin zuciyar ka, babu wata macen da zata kuma samin gurbi cikin zuciyar ka, ka mance da cewa Allah shi ne sarkin mulki mai yin yadda yaso da bayin sa, nasan ka da son yara amma son da kake yiwa waÉ—an nan yaran na daban ne, kana yi musu irin son da uba yake yi wa Æ´aÆ´an sa, haka ne ko?." tayi magaran tana duban sa da murmushi sosai kan fuskar ta. numfashi ya sauke kana ya janyo ta jikin sa sannan ya ce "Haka ne." ya faÉ—a dan babu É“oye-É“oye ko karya sakanin su, ko yan zu ma dayayi kokarin yin hakan sabo da wani dalilin yasha wuya sosai da fama da abun cikin zuciyar sa. wani yelwataccen murmushi ne ya baiyana kan fuskar ta, kana ta ce "Kana son ta?." kai ya gyaÉ—a alamar Eh sannan ya ce "Amma abar maganar domin bana jin zan iya haÉ—a ki da wata." gyemun sa taja, sai kuma ta É“ata fuska sannan tace "Haka Allah ya ce, bana son ka canza daga halin dana sanka baya yi maka kyau, dama kan haka kake masaltawa zuciyar ka aje damuwar da bata saba ba, shine har kake son ka koyi karya ko?, kana son ta, tun daga farkon labarin ta naji nima ina son ta ina son Æ´aÆ´an ta, ita ta musamman ce yarin ya karama mai halin man ya ba kasafai ake samun irin su a duniya ba, ni ma ina son ta, zan ku ci gaba da son duk wani abun da kake so har idan bai saÉ“awa Shari'a ba har karshen rayuwa ta zan cigaba da son sa." mike wa zaune yayi ya lankwashe kafafun sa kana ya dubi ta da É—in bin farin ciki da jin daÉ—in kasan cewar ta cikin rayuwar sa ya ce "Haki ka babu wan da yakai ni dace da samun mace ta gari, da ace kowani na miji irin ki ya samo a matsayin mata shi da damuwa ko tashin hankali bazai gansa ba har karshen rayuwa, Allah yayi miki albarka matar aljanna, faran tamin da kike Allah kema ya faran ta miki fara Æ´ar duma-duma ta." "Ameen Ameen ameeeeeen." tafaÉ—a tana jan É—an gyemun sa irin na gayun nan. sai kuma da sauri ta saki gyemun ta ce "Ka faÉ—a mata kana son ta kuwa?." kai ya girgiza ya ce "Ban faÉ—a mata ba." ta ce "To me ya sa?." ya ce "Sabo da baza ta amince ba." "Kamar ya, zakace bazata amin ce ba, baka tin kare ta da batun ba ka bata laifi." tayi maganar tana rike haÉ“a. kuma tun ta yaja kana ya ce "Um to tana da masifa tsiwar tsiya ce da ita." dariya tayi sosai tare da tafa hannu ta ce "Masifa haÉ—e da tsiwa kuma, a'a kada kayi wa kanwa ta fin tsayi." shiko murmushi yayi yana faÉ—in "Allah idan ta fara tsiwa sai kin sha mamaki." dariyar ta kuma ta ce "Zata amin ce kai dai je ka latsa ta kuma ka gani in sha Allahu zata amin ce, wata mace ce zataki tayin ka duk haÉ—uwar ta da dukiyar ta kuwa, ai mijin nawa da farin jinin sa aka halitto sa, shiyasa ma har gida ake kawo masa hari, wannan bazawarar taka ma jiya ta zo." dariya duk kanin su suka fashe da shi, zillo tayi gefe ganin yami ko hannu yana kokarin ruko ta, tasan sarai baya so tari yi masa maganar ire-iren waÉ—an nan matan da suke kawo masa hari. janyo ta yayi jikin sa ya rungume yana faÉ—in "Zakiyi baya ni." dariyar take tana daÉ—a shige wa cikin jikin sa. Kissing yashiga ai ka mata yana faÉ—in. "Hakika nayi dace da mace ta gari Æ´ar uwa ta jini kawa kuma abokiyar shawara, tabbas duk wan da yasa mi mata kamar ki yagama more yaruwar sa har gaba da abadan, ke matar aljanna ce insha Allahu da yar dar Allah zamu shiga aljanna ni da ke da kafafun mu." Baki ta turo gaba ta ce "To HAMDAH fa?." ya ce "To har da ita." mumushi tayi tare da daÉ—a rungume shi ta ce "In sha Allahu kuwa Allah ya tabbatar mana." ya am sa da amee. nan suka shiga nuna wa junan su tsantsar kauna da soyayya in da zancen ya sauya suka lula duniyar ma'aurata... Wane ne AHMAD?......! Mommyn Twins ce 8/19/22, 10:56 - Ummi Tandama😇: Ina fita daga cikin motar na shige cikin asibiti, batare da na jira fitar sa ba, yabuÉ—e wa su Nasmah yaruko hannun su suka biyo baya na, a kusan tare muka shiga cikin parlour'n asibitin. cike da girmamawa ma'aikatan asibitin suka shiga yi mana maraba da zuwa, direct office É—in Dr ya nufa bayan yace nazo mu shiga. kamar bazan bisa ba har sai da yakai bakin kofar office É—in kafin na biyo shi, Dr na ganin mu ya mike da sauri yana amsa sallamar da Ahmad yayi. Dr yace "Barkan ku da zuwa bismilla." yanuna mana kujeru biyu da suke fuskantar juna wan da suke gaban table É—in sa, sai da muka zauna kafin shima ya koma mazaunin sa, bayan gaisuwar da ya mika mana cikin girmamawa kana ya shiga yiwa su Naseem da suke like jikin Ahmad wasa. Dr ya dubi Ahmad yace "RankashidaÉ—e an shirya za'a iya gudanar da aikin yanzu?." yace "Eh." batare da É“ata lokaci ba Dr ya kirawo wasu Nurse's biyu mace da na jiki, in da macen taja jini na namijin kuma yaja nasa. muna nan zaune can da É—an jimawa suka dawo da Result É—in test É—in, suna mikawa Dr suka fita, Dr yashiga buÉ—e takardun, shiru yayi tare da duban mu dukkan mu kana ya kuma mai da idanunsa kan takardan, da sauri Ahmad da gaba É—aya yanayin sa ya sauya a Æ´an sakanni yace "Yaya dai Dr me ke faru!?." yayi tambayar da yanayin shiga damuwa, jim kaÉ—an Dr ya É—ago da murmushi yadube mu yana faÉ—in "Komai dai-dai babu wata matsala." Ahmad ya sauke wani dogon numfashi kana ya mike tsaye fuskantar sa É—auke da murmushi mai bayyana zallan farin ciki, Dr ya mika masa hannu yana faÉ—in "Allah ya sanya alkhairi yabada zaman lafiya." da sauri yace "Amen amee ameeeeeen ya rabbil izzati." ya mikawa kowa result É—in sa. har gurin mota Dr ya rako mu sai da muka shige mota sannan ya koma ciki. yaja motar muka fice daga harabar asibitin. har lokacin fuskarsa sa na bayyane da zallar jin daÉ—i da farin ciki,sai zuba murmushi yake. niko lokaci zuwa lokaci sai na ja karamar tsaki dan acike nake tam. ya juyo gefen da nake ya dube ni da murmushi kana ya mai da idanun sa kan titi yace "Kyakkyawa ta kin ji albishir mai daÉ—i ko, ina cikin farinciki sosai da kika sami kyakkyawar sakamako a kaina, ina da tabbacin zaki daÉ—a samin nutsuwa dajin inganci lafiya ta, baki ji yan da naji ba É—azu da Dr nan yayi shiru bai faÉ—i result É—in ba yana kuma kallon mu, tunani na É—aya ace nine keda wata matsalar shike nan nasan baza a bani ke ba, niko ban damu ace kina da wata matsala ba ahaka nake so kuma zanyi rayuwa da ke." annurin fuskarsa yakuma faÉ—aÉ—awa sannan ya kuma dubana yana faÉ—in "Kyakkyawa ta bazakiyi farin ciki da jin result mai daÉ—i ba dajin ingancin lafiya ta." baki na murguÉ—a nace "To ni inaruwana da wani ingancin lafiyar ka, mutum da lafiyar sa an sa yaje an wani É“ula masa jiki akarin banza, ." nayi kwafa ina kawar da kaina gefe. da sauri yace "Yihakuri Madam na tabbatar kina da lafiya dan kisan lafiya ta yasa mukaje asibitin ayi min afuwa a gafarce ni, juyo ki kalle ni ki tabbatar da gaskiya ta kinji kyakkyawa ta." daÉ—a kawar da fuskata nayi ina cuno baki gaba haÉ—e da murguÉ—a masa bakin, murmushi mai sauti yayi yana leko fuskata... awani katon ShopRite ya tsaya yajuyo gefen da nake yace "Kyakkyawa ta sauko mu shiga." ko kallo bai ishe ni ba bare yasa ran amsawa ta. tare da su Naseem suka shiga can suka fito niki-niki da kayan ciye-ciye... Muna isa gida tun kan ya karasa dai-dai ta parking nakai hannu jikin matfin motar zan buÉ—e najita gam, sai da ya dai-dai ta parking É—in batare dana dube sa ba nace "BuÉ—e min." nafaÉ—a a takaice, jin yayi shiru baiyi magana ba ya sani juyowa gefen da yake a kufule, karaf muka haÉ—a ido da sauri na janye ido na, shiko numfashi ya sauke tare da faÉ—in "kin ki faÉ—a min in da kike so ayi shagalin bikin mu." "Da zai fi maka karike tambayar ka kadai na dami na da ita, danni babu abin da zai kai ni gurin wani biki." ya ce "Shike nan an daina damin ki duk yan da kike so haka za'ayi, wai duk wannan lallen wani akayi kai gaskiya naji daÉ—i na, amma yayi kyau sosai fa, shine ba'a faÉ—a min nabada kuÉ—in lallen ba bayan an san hakki nane, kawo na kara gani dole ma na biya kuÉ—in sa." yakai hannu ya kamo nawa yana cigaba da faÉ—in "Kice zan sha kallo gobe amma bari na fara tun yau." da sauri nayi yunkurin fisge hannu na jin wani irin shock lokaci goda ya sarga min, sai dai yan da ya rike hannunan ban sami damar iya fizge wa ba. "Sake min hannu Malam kabuÉ—e min kofa nafita." nafaÉ—a ina ta kiciniyar kwatar hannun nawa. yace "To naji amma muga wayar ki." "Adalilin me zan baka waya ta?." "Aro zaki bani yanzu zan duba abu na baki." gyara rukon wayar nayi a É—aya hannu na na É“ata fuska nace "Ka sakar min hannun kakuma buÉ—e min kofa." numfashi ya fesa yajuya baya ya dubi su Naseem gaba É—aya hankali su na kan kallon katun É—in da ya saka musu a wayar sa tun fitar su daga ShopRite É—in nan. kana ya dawo da kallon sa gare ni a hankali yaÉ—an rankwafo in da nake har ina jiyo kamshin sa sosai, idanu ya lumshe tare da kuma buÉ—e wa a kaina, da sauri na rumtsa idanuna ganin yana ta kokarin saka nasa cikin nawa, ga yan da yamatso ni sai nake jin jikina yayi min nauyi wani abu mai kamada kasala nata kokarin ziyartata, "Ka sake min hannu ka buÉ—e min kofa." nayi maganar cikin É—an É—aga sauti yayin da idanuna ke rumtse. yace "Zan sake ki zan kuma bude miki bayan kin bani aron wayar ki." da sauri na mika masa wayar dan yana yin yanata daÉ—a shiga ta. ya amshi wayar tare da sakar min hannu, a tare muka saki numfashi mai sauti, nayi saurin gyara zamata na matsa tajikin kofa sosai. shima zaman nasa ya gyara kana yashiga latsa wayata daga bisani yaÉ—au É—ayan wayar sa shima ya daddanna sannan ya mika min wayata yana faÉ—in "Na biya kuÉ—in lallen da aka tsara min É—in nan." yana rufe baki kuwa saiga shigowar alat na 1 million. fuska na yamutsa, shiko murmushi yayi tare da buÉ—e min kofar, nafita da sauri ina tafiya ina kunkuni, bayan na yabi da murmushi har na É“acewa ganin sa, yafito ya buÉ—ewa su Nasmah yace musu su shiga ciki shi bari ya tsaya yayi salla dan lokacin ana kiran sallar magriba... Ina shiga na tadda su Aunty Nasiba natakan ai ki sukayi min barka da dawowa na amsa inayi musu sannun su da aiki. koda na haura sama kayan jikina na narage sannan na fita na shiga É—akin da su Hajiya Lubabatu suke, tana ganina tace "Yanzu nake kan maganar ki yauce rana ta karshe ga sauran kayan ki da yawa ga su dai na haÉ—a karÉ“i kisha yanzu cikin dare kya karasa sauran." tamika min cup mai haÉ—in magunguna ciki, na karba ina yamusa fuska na sha nan ta sani na kwaÉ“e kayana tashiga mulke ni da wasu sinadaran, har wajen karfe biyu na dare idanun mu biyu dan a daren akayi min gyaran gashi, bamu muka kammala komai ba sai wajen karfe huÉ—u na asuba bayan ta wanke ni da ruwan turare nan na wuce É—aki na, nafaÉ—a gado dan gaba É—aya idona rufewa yake sabo da tsabar bacci, na gyara kwanciya ta ina kunkuni kasan raina "Haka kawai a hana mutum bacci akan karin banza." batare da É“ata lokaci ba bacci yayi awon gaba da ni.... Can cikin bacci najiyo muryar Faty tana bubbugani da kiran suna na, mika nayi tare dayin salati na bude idanuna. fuska na É“ata nace "Faty meye haka mutum yana baccin sa zaki kama tada ni." kai ta langwaÉ“ar gefe tace "Ayya Adda HAMDAH kiyi hakuri Bappa ne yace nazo na tada ki yayi ta kiran wayar ki baki É—auka ba." a hankali na mike zaune tare da kuma yin mika haÉ—e da salati, na dubi agogon dake like da mirror karfi 12:30, ido na waro nayi mamakin ganin yan da lokaci yatafi haka. janyo wayata dake karkashin pillow nayi ido na waro kan wayar ganin missed call É—in Bappa yacika wayar. da sauri na sauko a gadon na É—au katuwar jijabin sallah ta na zura nayi waje Faty ta biyo naya na, wani irin daddaÉ—an kamshi ne yaziyar ci hanci na san da na kusa kai na cikin parlour, an gyara ko ina sai kamshi ke tashe, babu kowa cikin parlour'n sai kamshi da sanyin da ke tashi ciki. step na nufa da É—an sauri, na sauka kasa mutane ne tam cikin parlour'n ka da wan da na sansu da wan da ban sansu ba, a sakiyar parlour'n kuwa wasu zuka zukan akwatuna ne da suka kai set 6 kaloli daban-daban, Inna Wuro na zaune gaban akwatunan tana gani na tayi min murmushi, nima na mayar mata tace "An tashi ne HAMDAH?." nace "Eh Inna inasu Nasmah ne?." tace "Ai yau su Nasmah ba zama anayi musu wanka suka fita wai Daddy'n su na jiran su a waje." kai kawai na jinjina. can na hangi su Hajiya Rahama da Hajiya Lubabatu suna ta nuna wa wasu mata kusurwa-kusurwan cikin parlour'n in da zasu kunna turare. nayi musu sannu na wuce su in da wasu suka bini da guÉ—a suna faÉ—in "Kaga amarya ta fito hasken ta ya bayyana." banbi ta kansu ba nayi waje. ina shiga side É—in su Bappa na taddashi tsaye yana gyara zaman babban rigar jikin sa yana gani na yace "HAMDAH ina kika saka wayar ki nayi ta kiran ki baki É—agawa?." nace "Bappa bacci nake." yace "Ina takardar sakamakon da likita ya baki jiya a asibiti? ga mutane can an fara hallara ana idar da sallar juma'a za'a É—aura gashi lokaci ya tafi É—aya saura yanzu yi maza ki kawo min." wani irin rass naji gaban kirji na ya yanke jiki a sanyaye nace "Yana É—aki." yace "Yi maza ki kaso min." nan da nan naji jikina yayi mugun sanyi, na dubi Faty nace "Faty je ki É—aki zakiga takarda kan mirror ki É—auko." tace to ta juya da sauri ta fita. niko a hankali nayi baya nazauna saman kujera dan gaba É—aya jikina yagama sanyi har nake jin jikina nason yayi wa kafafu na nauyi, a bun da nake ganin sa kamar wasa dai gashi nata kokarin zamowa gaskiya. lura da yanayin da na shiga yasa Bappa yashiga yimin nasiha, ina dai jin sa amma gaba É—aya hankali na baya gunsa. batare da É“ata lokaci ba Faty ta dawo rike da takardan, ta mika min nikuma na mikawa Bappa ya amsa da sauri ya fita. nakai tsawon minti goma zaune a gun daga bisani na mike a hankali na fita na koma side É—ina. koda na shiga bedroom É—ina akwatunan dana gansu a parlour'n nan su nagani jere cikin É—akin, kan gado nabi da kallo, wani dankararren leshi ne haÉ—e da gyare da jaka da takalmi,da sarka da Æ´an kunne da abun hannu mai sheki da É—aukar ido, turo kofa akayi da sallama Hajiya Rahama ne ta shigo ta dube ni tana faÉ—in "Ƴan uwan Ahmad suka kawo akwatunan nan kina bacci yasa ba'a É—agaki ba, amma anyi musu sallama da tukuici na musamman, na sending musu 500k ta account É—in su, an haÉ—a su da drinks katon ashirin haÉ—e da cincin da diblan da akayi jiya na ba'i sai dai babu yawa tun da ba'a san da zuwan su ba, boket shida ne kawai, yanzu nasa a karayin wani saboda wan da za'a baiwa ba'i, hakan yayi dai ko?." nace "Yayi sosai ma bani account number ki na samiki kuÉ—in." tace "A'a nima gudumawa ta kenan kibarshi, ga kaya nan an cire miki sai kiyi wanka ki saka." nace to tare da yi mata godiya, tajuya ta fita, na tuÉ“e hijabi na na shige bayi, wanka sosai nayi na kimsa jiki na da kyau sannan na fito, gaban mirror na zauna nashiga mulke jikina da mayuka masu daÉ—in kamshi haÉ—in hajiya Lubabatu, simple make-up nayi amma nayi kyau sosai dan nasha gyara sosai ga kyan halitta ta da ubangiji yayi min. a hankali na mike na isa in da kayan yake na É—ago su na soma sakawa, É—in kin leshin riga da zani ne tsarin É—in kin yayi, bayan na saka kayan na É—au sarka da Æ´an kunnen nazo gaban mirror na saka,sannan na murza É—aurin É—ankwali, a hankali nabi jikina da turare natsaya ina kare wa kaina kallo tacikin mirror. Kamar daga sama najiyo sautin babban masallacin unguwar mu ana faÉ—in "Fatihaaaa Allah yayi aure ya É—auru Allah ya bada zaman lafiya da zuriya É—ayyiba." kirji na ne yayi wani irin bugawa da har sai da na kai hannuna na dafe kirjina, wani irin jiri ne ya É—ibe ni na kwalla kara tare da zubewa kasa na rushe da kuka mai matukar tsuma zuciya tamkar zan shiÉ—e. Faty ce ta shigo ta sha wankan ta rike da É—ankwali a hannu Aunty Nasiba ta dube ta cike da zulaya tace "Duk a cikin gayen ne haka rike É—an kwali a hannu." dariya tayi tana faÉ—in "Gun Adda HAMDAH zani ta É—aura min." ta haura sama ta tura kofar da sallama da sauri ta karaso cikin É—akin ganin yan da na haÉ—e kai da guiwa nake ta faman rusar kuka, tashiga girgizani tana faÉ—in "Adda HAMDAH me ya same ki?." ban iya bata amsa ba sai sautin kuka na daya karu, a kiÉ—ime ta sake ni tayi waje, tun daga saman step tashiga kwaÉ—awa Inna Wuro kira, sabo da hayaniyar jama'a yasa Inna Wuro bata jiyo kiran ba, da sauri Faty ta karasa sauka tazo in da Su Inna Wuro ke zaune ta ruko hannun ta tana yi mata nuni da sama da faÉ—in "Adda HAMDAH." "Me ya sami HAMDAH!?." Inna Wuro tayi tambayar hankali tashe ganin yan da Faty'n ta ruÉ—e tana nuna hanyar sama ta mike tsaye da sauri ta haye sama Faty na biye da ita. Ina durkushe a gurin har lokacin kukan nake kamar raina zai fita. hankali tashe Inna Wuro tashiga faÉ—in "Subhanalillahi HAMDAH lafiya me yasame ki?." ta É—ago kaina dana haÉ—e da guiwa, sai kawai na zube a jikin tare da kuma fashewa dawani sabon kuwa, cikin muryar kuka sosai nake faÉ—in "Inna Wuro wai da gaske an É—aura auren Inna Wuro ina jin tsoro suma zasu cutar dani." bayana tashiga bubbugawa jiki a sanyaye ta gyara zaman ta a kasan tadaÉ—a kwanto da kaina bisa kafar ta tashiga rarrashi na da kalamai masu kwantar da hankali haÉ—e da natsiha mai shiga jiki da karfafa guiwa. har sai da taga nayi shiru hankali na yado jikina kafin ta fita a É—akin ta barni ni da Faty da itama tagama shan kukan ta... Har yamma ina daki ban fito sai wajen sallar magriba bayan nayi wanka na sauko kasa, nan na tadda mutane sunanta watsewa, Hajiya Rahama da Aunty Nasiba nata sallamar mutane da kayan tsaraba. nan na shiga tayasu har jama'a suka watse, yarage Hajiya Rahama da Aunty Nasiba da Hajiya Lubabatu, bayan sallar isha Hajiya Rahama da Hajiya Lubabatu sukace zasu tafi, har gurin mota muka raka su ni da Aunty Nasiba, nayi ta musu godiya sosai bayan na sallami Hajiya Lubabatu da kuÉ—i mai tsoka. sai da mukaga tashin su kafin muka juya, a tsakiyar gidan muka rabu da Aunty Nasiba tace min zata wuce sashin su Inna Wuro acan zata kwana, nayi-nayi mukoma side É—ina mukwana a can taki. koda na koma ciki na tadda su Zulai sunata daÉ—a gyara cikin side É—in suna gamawa suka tafi É—aya side É—in dan tun ranar da aka zuba sabbin kaya suka kwashe kayan su suka koma can. tuni Naseem da Nasmah suka yi bacci saboda gajiya dan tun da safe da suka bi Ahmad ban sake sasu a idona ba sai yamma. É—akin su na shiga na gyara musu kwanci tare da yimusu addu'a sannan naja musu kofa na fita na koma É—akina.... A É“angaren Ahmad kuwa, cikin gidan sa cike tam yake da jama'a shigowar sa kenan cikin parlour'n sa bayan ya sallami wasu ba'in sa, jama'a sai zolayar sa suke dayi masa kirari, É—aya daga cikin É—akunan da suke cikin parlour'n ya shiga, wasu manyan mata ne zaune cikin É—akin yakaraso ya zauna tare da gaida su, suka amsa sunayi masa ya gajiyar hidima. É—aya daga cikin matan ya mai da hankalin sa gare ta yace "Hajiya naga kiran ki É—azu ina tare da jama'a ne." tace "Eh dama na kira ne naji wata shirin ake kanyi na É—auko amaryar naga dare nadaÉ—a yi ne, ga jama'a sun fara watse wa." murmushi yayi tare da faÉ—in "Ai Hajiya wannan amaryar baza ta É—auku ba abar masu tafiya sutafi abin su kawai." tace "Kamar ya ba zata É—auku ba?." zaman sa ya gyara sannan yace.......! Mommyn Twins ce 8/19/22, 10:56 - Ummi Tandama😇: HMD WASA FARIN GIRKI NA RASHEEDAT S DIRECTOR Ganin yan da nayi maganar da alaman shiga firgici dajin cewa Ahmad ne wan da Bappa ya karÉ“i sadakin sa, sai yayi saurin tarar numfashi na da faÉ—in "Eh Ahmad in ban da abin ki HAMDAH ace mutum kamar Ahmad yataho niman auren ki ai abun alfahari." "Bappa ni wannan mutumin fa.." sai kuma nayi shiru batare da na karasa faÉ—an abin da zan faÉ—an ba. murmushi Bappa yayi tare da girgiza kai ya ce "Shi mutumin me yayi, kada kice komai kiyi addu'a zakiga alkhairin sa da yar dar ubangiji." shiru nayi ban kuma cewa komai ba amma a kasan raina sam banji daÉ—in lamarin ba, a tunani na ma wani ne daban yakawo sadakin ashe wannan É—an anacen ne me shegen naciyar tsiya, wato dana ce yatafi da kuÉ—in sa shine yazo gurin Bappa ko. kwafa nayi ina ciza laɓɓana na kasa. haka Bappa yayi ta min nasiha, ina dai zaune ina jinsa sai da ya gama kafin na mike nafita... Bayan kwana Uku Ahmad ya dawo gurin Bappa da tambayan sa rana, Bappa ya bashi wata É—aya yace ya dawo bayan wata É—aya a É—aura auren. Ina zaune a parlour ya shigo da salla, su Nasmah suna ganin sa sukayi gurin sa a guje, kamar kullum haka yayi ta biyewa shiriritan su. daga bisani ya juyo in da nake, in da nayi kamar bansan yana gurin ba. ganin irin kallon da yake min yasa ni jan guntun tsaki, idanun sa ya lumshe tare da sake buÉ—e su a kaina kana ya É—an saki murmushi yace "Kyakkyawa ta albishirin ki." ban ko juyo in da yake ba bare ya sa ran cewa zan tanka masa. murmushi mai bayyana zallan nishaÉ—i da jin daÉ—i ya sake sannan yace "Wata É—aya Bappa Malam ya yanke min na bani ke, duk da yayi min nisa amma ina cikin farin ciki sosai, ke ya kama ta ki yanke min kwanakin amma sam kin ki saurara ta da lokacin bazai kai har haka ba, shi kuma ina jin nauyin sa, kin ga abin da kika jamin ko." É—an sakai ta maganar nasa yayi kana ya mike tsaye, zato na tafiya zaiyi sai gani nayi yadawo kujerar da nake ya zauna,tare da leko fuska ta. kawar da fuskata nayi gefe, yasaki murmushi mai sauti tare da faÉ—in "Yakamata kibani aron lokacin nan naki mai tsada aro nace ba kyauta ba Please, zan maida miki kayan ki da zaran mun gama tattaunawa kan batun hidimar auren mu, wace Kasa kike so muje a gudanar da shagalin bikin mu, dan Kawa tace bai kamata ayi bikin a Nigeria ba, wani kasa kike so aje a yi acan." fuska na haÉ—e na ce "To ni me yada meni ina ruwana in yaso ayi a sama ba'a doron kasa ba." Ido ya É—an waro yace "A sama kuma? wane mu ai bamu kai nan ba." baki na murguÉ—a nace "Kada ka kaini da nisa dama yaushe kazo bare ka isa, ai sai isassu, saka saki nake nufi ba'a sama ba a kasa." "Uhm igiya zaki É—aura mana muna lilo koko a jirgin sama." baki na kuma murguÉ—a wa namike ina kokarin barin gurin. da sauri yace "Baza a bani aron lokacin ba kenan kyakkyawa ta?." ban ko kulashi ba nayi gaba abina..... Tun daga ranar kullum sai yazo bakuma zan kulashi ko na saurarare ba, hakan kuma bashi zai hanashi hobe ya fasa zuwa ba. ana saura sati biyu bikin Hajiya Rahama matar ministar Bukar tazo, bayan mun gaisa nasa aka cike ta da kayan abinci da sha, tana ci muna É—an taÉ“a hira cikin hirar take cewa "Hajiya HAMDAH kin kimu ko nima a waya bare zuwa gida, sai kawai kwasam nasami labarin wai zakiyi aure abun farin ciki wai Ahmad Tijjani Sabil zaki aura, wlh kar kiga yan da nayi farin ciki amma nayi fushi wai sai a bakin wasu zan ji ai ko a waya zaki tura min da sako." Muemushin yake nayi nace "Ayi min afuwa wlh abubuwa ne zukayi yawa sai a hankali yanzu." tace "Haka ne kam shirye shiryen biki ga harkokin kasuwan ci abun kam sai a hankali,shiyasa nayi miki uzuri na taso na taho da kafata, Allah ya sa ayi da mu." zaman ta taÉ—an gyara sannan ta kalli gefe da gefen cikin parlour'n kana cikin kasa da murya tace "Amma ya banga karin wasu ma'aikata cikin gidan nan ba, ko zuwa suke su zo." cikin rashin fahimtar abib da take nufi nace "Wasu ma'aikatan kuma ai Talatu da Zulai sun wadaci ai kin cikin gidan nan." tace "Ba waÉ—annan ma'aikatan nake nufi ba masu gyaran jiki na amare." baki na taÉ“e nace "Masu gyaran jiki kuma, babu wasu masu gyaran jikin da a kayyato." ido ta waro tare da faÉ—in "Wai kina nufin aure saura sati biyu baki fara gyara ba?, kin san wa zaki aura kuwa?, mutumin da akace matarsa ta mallake sa sai yanda tayi da shi, to wlh yakama ta ki farka tun da wuri kisan abun da kike ciki." "Uhm nifa babu wani gyaran jikin da zanyi a barshi kawai." tace "Mene kan kishiya zaki shiga kice bazakiyi gyara ba, matar da ake faÉ—an ta kowa sai yabada labarin ta, to ko ba komai bace ita ace mutum kamar Ahmad Tijjani Sabil ai dole ayi gyara sufa irin waÉ—an nan manyan mutanen tanan ne kaÉ—ai zakabi ka mallake su, tun da kai ba hanyar shirka zakabi ba, idan ita da ake labarin nata tana yi sai taje can taci gaba da yi, kai ma dai baza'a barka a baya ba, akwai tawa shahararrir mata wacce ake kiran ta da Dr mata Hajiya Lubabatu tana da ma'aikata da dama tana tura su gari ya gari, ta kware wajen iya gara Yakamata a gaiyatota ba ma'aikatan taba ita da kanta tazo, hausawa suka ce idan kana da kyau kakara da wanka, Yakamata kiyi huɓɓasa kifarka da wuri, bari yanzu ma na nime ta." tana kaiwa nan taÉ—aga waya ta daddanna ta kara a kunne, jim kaÉ—an ta soma magana nidai ina jin amma sam ni ban so takira wata ba danni ban sa auren a ka ba. bayan sun gama wayan ta dube ni tace "Mun gama magana da ita zatazo gobe, dan ma yau tana gurin wani aikin ne amma tace zata aje Æ´ar aikin ta acan ita zata zo nan, dan na faÉ—a mata ko wace ce ke sai ki zauna da shiri gobe zamuzo da ita, zanbi gidan ta na É—auko ta gobe idan Allah ya kaimu." "Allah yakai mu." nafaÉ—a a takaice.. Washegari da safe kamar yanda Hajiya Rahama ta faÉ—a sai gata da Hajiya Lubabatu, Hajiya Lubabatu ta bukaci dana ware mana É—aki guda domin gudanar da aikin ta, É—aya daga cikin É—akunan sama nan muka yada zangon mu,batare da É“ata lokaci ba ta fara gudanar da aikin ta. ranar sai da nayi kuka tuno da Aunty Rafee'at da Hajiya Lubabatu ta haÉ—a magunguna cikin cup ta ce nasha, sai na tuna ranar data kawo min magunguna a gidan Ya SALEEM tace daga hannun shahararriyan nan aminiyar ta Asma'u Jos ya fito, ranan nayi kuka sosai tuno da ahlina, Hajiya Lubabati tayi ta rarrashi na da tambayar abin da ya sameni sai dai ban bata amsa ba da kyar ta shawo kaina nayi shiru, sannan taci gaba da aikin ta. kwanan mu goma da Hajiya Lubabatu, duk wan da ya ganni sai sambarka, ni kai na nasan na sauya sosai, nakara kyau na kara cika ko ina na ya cika tup-tup, kullum muna tare da Hajiya Rahama da wasu kawayen ta, dan acewar ta itace babbar kawa ni dai ina biye mata a haka dan Hajiya Rahama ba sa'ata bace ta girme min nesa ba kusa ba. Bana fita kullum ina É—aki in nafita kuwa to iyakata parlour'n sama, kamar yanda Hajiya Lubabatu tace bazan fita ko nan da can ba har sai ta gama aikin ta. shiyasa ma na sami sa'ida daga gun wannan É—an anacen dan ko yazo iyakar sa parlour'n kasa yakaraci zaman sa yatafi dan bana sauka. ana saura kwana uku bikin ranar tun da safe Hajiya Rahama da kawayen ta suka zo, Aunty Nusaiba matar Uncle Mahmoud itama da wasu kawayen ta sukazo, su Inna Wuro da Faty duk muna tare da su a side É—ina, abin ka da taro ko babu yawane sai kaji hayaniyar nan ai ko parlour'n sama da kasa duk ya dauki hayaniyar jama'a. wasuyan motoci guda biyar suka shigo gidan masu É—auke da tambarin sunan Company'n Ahmad Sabil. duk kanin su shake suke tam-tam da kaya. shigar su ke da wuya kira ta shigo wayata, koda na duba mai kiran ganin bakuwar lamba ce, kamar bazan daga ba sai da kiran takusa yanke wa kafin na É—aga da sallama, daga cikin wayar numfashi naji an sauke kana daga bisani a ka soma magana "Kyakkyawa ta barka da safiya inad fata kina cikin koshin lafiya ke da yarana gaba É—aya." Shiru nayi batare da na amsa shiba sai murguÉ—a bakin da nayi kamar yana kallo na. yacigaba da faÉ—in "Ga ba'i a waje suna niman izinin shiga." kashe wayar nayi ina kunkuni kasa-kasa "To ina ruwa da an hana ba'in shiga ne ko kuma wani sabon sai da hali ne." Aunty Nusaiba dake kusa da ni tafube ni tana faÉ—in "Wasu ba'i kuma?." baki na turo gaba nace "Wai wannan Ahmad É—in ne wai wani wai ga ba'i a waje ko da an hana su shiga ne da zai wani kira yana faÉ—a wa mitane." tace "A'a kodai motocin da yanzu naji shigar sun nan ne naga mutane tsaye a jikin motar wata kila sune ba'in to ace su shigo mana." Faty tashiga kwallawa kira Faty dake É—akin su Naseem tafito parlour da sauri tace "Yi sauri kije kicewa mutanen da suke wajen nan su shigo sai ki sauke su a parlour'n kasa." tace To, jim kaÉ—an ta dawo tace sun shigo suna parlour, Aunty Nusaiba ta sauka taje ta same su. bajimawa ta dawo tace min "Masu ai ki ne wai Ahmad Sabil ne ya turo su wai zasu fita da kayan cikin side É—in nan su shigo da wasu." kafin nace wani abu Hajiya Rahama tace "To bismilla su fara mana, sai su fara daga kasan idan suka gama sai a koma kasan a basu guri su gyara nan É—in." tace "To haka ko za'ayi." ta juya ta koma domin sanar musu. a raina nake faÉ—in "Kamar wani an sashi ni shishshigi ne bana so." Batare da É“ata lokaci ba ma'aikatan da suka kai wajen rai goma dukan su maza ne suka fara gudanar da ai kin su, kan kace me sun gama kwashe kayan cikin parlour'n kasa, kama daga kujerun cikin parlour'n, bed and bedside drow dressing mirror wardrobe dake cikin bedrooms É—in parlour'n, zuwa kayan kitchen and dinning. kaf sukayi waje dasu suka jibge su cikin É—aya side É—in cikin gidan da bakowa ciki. nan suka rinka shiga da kayan da suka zo dasu a mota suna shirya komai yan da ya kamata. zuwa karfe 1 sun kammala komai sun shirya komai a inda ya kamata. nan suka bukaci haurawa sama domin cigaba da aikinsu, muka dawo kasan muka basu guri. lokacin dana sauko kasa sai nazamo Æ´ar kallo tamkar ba parlour na dana sani ba abun ba'a cewa komai tsaruwar sa ya wuci misali, kowa sai tabawa da sam barka yake.... Sai wajen yamma suka gama kammala komai sukayi mana sallama suka tafi. abin kamar karya nake ganin shi sai daÉ—a zamowa gaske yake,ana gobe É—aura aure Ahmad yaki rani lokacin ana yimin lalle, naki É—agawa sai da yayi min missed call biyar kafin na É—aga, yace "Madam gani na shigo fito muje asibiti a bincika miki lafiya ta." "Meye damuwa ta da lafiyar ka." nafaÉ—a tare da kashe wayar. ina kallon wani kiran nasa na kuma shiga haka naki É—agawa, ga haushin lallen da aka bi aka dame ni da shi nifa in da anbi tanawa da duk waÉ—an nan fidda ficen da an barsu. tsaki naja jin wani kiran ya kuma shigowa a fusace na É—ago wayar niyyata na gaya masa magana idan bai dai na dami na ba, sai naga number Bappa ne ya bayyana kan Screen É—in wayar, da sauri naÉ—aga wayar tare da yin sallama Bappa yace "HAMDAH fito kuje asibiti ga Ahmad na jiran ki, kinsan yanzu ba ayin aure sai da gwajin lafiya kuje ku gwada lafiyar ku sabo da sai da shi yanzu ake yin aure, kafin a É—aura aure gobe dole sai an bukaci takardar shaidar ingancin lafiyar ku wan da yafito daga hannun likita." nace "Bappa lalle ake min kuma yanzu akayi bai bushe ba." yace "To bari ace yatafi in yaso anjima sai ya dawo." To na amsa da shi a takaice... Sai bayan sallar la'asar kafin lallen yabushe aka wanke, duk nabi na gaji, a gabiye na faÉ—a cikin bedroom É—ina, nashige cikin bayi domin yin wanka nakuma gyara jiki na, dan naji alamar zuwan al'ada ta. shi yasa nace wa Hajiya Lubabatu zanje É—aki na na É—an watsa ruwa acan na huta dan nagaji da yawa, ina gama kimsa jikina nafito, gaban mirror na zauna nasoma shafa haÉ—in mayuka masu daÉ—in kamshi data haÉ—a min. waya ta ce tashiga ruri ganin mai kiran yasa nayi banza, yayi ta kira yafi a kirga ban É—aga ba. knocking akayi tare da yin sallama daga bakin kofa, jin muryar Faty ce yasa nace tashigo. tace "Adda HAMDAH wai kizo inji Yaya Ahmad." fuska na É“ata nace "Kice bazan zo ba." har takai bakin kofa nace "Bappa na gida ne?." tace "Eh." nace "Kice masa ina zuwa." ta amsa da to tayi waje. tsaki naja a fili nace "Wlh badun kada Bappa yace naraina sa ba Allah da ba abin da zaisa naje." sai da nagama iya yanga ta kafin nasaka kaya nafito ina gyara mayafin kaina, su Nasmah na ganina suka biyo ni da gudu suna faÉ—in "Mommy damu biki." Aunty Nasiba dake parlour'n kasa tana tare da masu aiki suna ta shirya abinci, nace mata zamuje asibiti tace "A dawo lafiya Allah ya tsare." nace "Amin." nayi waje su Naseem suka biyo ni suna cigaba da faÉ—in zasu bini.. Yana zaune a mota yana ganin mu tun kan mukaro ya fito acikin motar. ihun murna yaran suka sake sukayi gurin sa a guje suna faÉ—in "Laa Daddy yazo oyoyo Daddy." ya buÉ—e hannun sa suka faÉ—o jikin sa ya rungume su yana dariya tare da bin ko wannen su da sumbata. na karaso gurin fuska ta É—aure tamau, yasake yaran yana faÉ—in "Kuzo mu buÉ—e wa Madam mota kada ta gaji da tsayu." yazaga É—aya barin ya buÉ—e yadube ni dakyau sannan yace "Kyakkyawa ta bismilla taho ki shiga." yayi maganar tare da nuna min hanya da hannu yayin da É—aya hannun sa ke rike da marfin motar. fuska na yamutsa namatso jikin marfin motar, ganin yana tsaye daf da in da zanbi nashiga cikin motar, sai na ja natsaya tare da naÉ—e hannaye na a kirji. murmushi ya yi kana yaÉ—an ja da baya kaÉ—an tare da faÉ—in "Bismillah Madam." baki na taÉ“e nashige cikin motar da bismilla. yamai da marfin ya rufe. tuni su Naseem sun shige gidan baya sai tsalle-tsalle suke. yazaga gefen direba ya shiga ya ja motar a hankali yayi hon mai gadi ya buÉ—e get yasa kai yafita a hankali. A hankali yake tukin kamar mai tautsayin kasa, yayin da su Nasmah keta zuba masa surutu yana biye musu, lokaci zuwa sai ya juyo ya kalle ni, niko na É“ata rai nayi kamar bana cikin motar. sai da naji ya gyara parking kafin na É—ago, *HAM'NAS* International Hospital na ganmu ciki. maganar sa najiyo yana faÉ—in "Mushiga kyakkyawa ta ko na sauko na buÉ—e miki ne?." tun kan yarufe baki nayi saurin É“alle marfin motar nafita ina jan karamar tsaki........! Mommyn Twins ce 8/19/22, 10:56 - Ummi Tandama😇: *HMDH* *WASA FARIN GIRKI* *NA* *RASHEEDAT S DIRECTOR 17 Yace "Hajiya za'a É—auko ta amma ba yauba sai bayan É—an wani lokaci." Hajiyar takarkata baki tana faÉ—in "Aure jibge kayi ne? yo in ba haka ba ace duk girman gidan nan ba rashin É—aki ba ba komai ba, kayi aure kabar matar ka wani waje bazaka haÉ—a kan iyalen ka guri guda ba, ko gimbiyar taka ta hanaka kawota gidan ne?." yace "Hajiya ita kuma meye nata a ciki, ai in da wan da yake son auren nan ma to bayan ta ne, wani É—an karamin dalili ne kawai yasa yau baza a É—auko ta ba." tace "Eh ai dama ita bata laifi badai ta yi sake an yi auren ba ai wayon ta ya kare." Murmushi Rasheedat data sako kanta cikin É—akin ta sake dan duk abin da suke a kan kunnen ta,ba farau bane hakan gun Hajiya da dangin ta, a koda yaushe gani suke ta mallake shi sai abin da tace zaiyi, ko wannan auren ma dasuka jishi lokaci guda sunyi matukar murna acewar su yanzu ne zai auri mata ita kam itace mijin shine matar,duk da dai bahaka suka so ba sai dai babu in da suka iya haushi da sanar Rasheedat shi yasa su yin murnar auren nasa. gani suke ta gama mallake sa sai abin da ta ce tahana wasu shigowa suci arziki, ita ba haihuwa ba, Hajiya Karima itace Uwar gidan Alhaji Tijjani Sabil wato mahaifin Ahmad, wacce yanzu yake kallon ta a matsayin uwa, tun kafin ya auri Rasheedat Hajiya Karima taso haÉ—a shi da É—iyar kanin ta wacce take hannun ta suna tare duka da Rasheedat É—in a gidan mai suna Sakeenat, yaki amin cewa yace sai Æ´ar uwar sa ta jini, duk yan da Hajiya Karima takai ga shiga da fitan ta haka Ahmad yaki sam yake kuma Allah bai bata ikon juya shi ba. karshe dai haka ta hakura badun taso ba, a É“angaren Sakeenat ma kuwa tana son Ahmad kamar tayi yaya har kuma gobe tana son sa, sabo da shi taki zaman auren da aka mata ko yanzu da take zawarci tana fata da burin mallakar Ahmad, sai dai abune mai wuya dan ko gaisuwar ta baya amsawa... Rasheedat ta karaso cikin É—akin ta dire babban tray da aka shirya musu abincin su ciki, kana tayi musu barka da warhaka, a yatsine hajiya Karima ta amsa bai dame ta ba tana dago wa suka haÉ—a ido da Ahmad suka sakarwa junan su murmushi. kana tayi waje. wayar sa ce tayi kara ya É—aga kiran sannan ya mike yafita. Da sauri ya bi bayan Rasheedat dake kokarin shiga corridor dazai sadata da side É—in ta, ya ruko hannun ta ya janyo ta sukayi gefen sa suka shige cikin bedroom É—in sa, suna shiga É—akin ya janyo ta jikin sa ya rungume tare da marairaice murya ya ce "Wash Kawa nagaji." gemun sa ta ja tace "To yau dai bazan ce ma sannu ba dan yau rana ce ta musamman gajiya dole." fuska ya marairaice yace "Haka zakice?." tace "Haka na faÉ—a, muje na tayaka wanka kanwata nazaman jiran ka, dan kasan dai kai zakaje ba dai ita tazo ba." murmushi yayi tare da shafo gefen fuskanta yace "Hukuncin da aka yanke min kenan?." tace "Har ya zartu ma kuwa." a tare suka saki dariya, nan tashiga taimaka masa yarage kayan jikin sa kana suka faÉ—a bayi, ta taimaka masa yayi wanka kana suka fito, nan ma ta tayashi sa kaya sannan ta bisa da turaruka masu daÉ—in kamshi. gaban wardrobe ta isa ta buÉ—e ta ciro jaka mai É—an girma sannan ta rufe ta buÉ—e É—aya gefen tashiga ciro kaya tana zubawa cikin jakar, ido ya zuba mata ganin yan da take aikin zuba kaya cikin jakar yace "Kawa ina za'a kai kayan kuma?." bata bashi amsa ba har sai da ta cika jakar tam da kaya kafin ta juyo ta dube shi tace "Ina zuwa." ta fita jim kaÉ—an ta dawo da mayafi a kanta ta ruko hannun sa tare da faÉ—in "Taso muje na raka ka duba kagani har karfe 11 saura." yace "Kawa ina kuma?." tace "Ina kuwa in ba gidan HAMDAH ba ko kasan cewa lokacin ta kake shiga, yanzu haka tana can tana zaman jiran ka." ido yaÉ—an waro yace "Shine da wannan katuwar jakar kamar wan da ake kori na." tace "Eh ayau kam kusan haka din ne." Ta janyo hannun sa tare da É—aukar jakar sukabi ta kofar baya,É—aya daga cikin motacin sa suka shiga ya jasu a hankali suka fita. a hanya ta sashi ya tsaya ya siya gasassun kaji kafin suka wuce. suna isa bakin get din gidan yayi hon masu gadi suka buÉ—e masa, yakusa hancin motar ciki yana dai-dai ta parking suka fito a tare, tana rike da jakarsa inda shi ke rike da laidar gasassun kajin da suka tsiya, suka nufi side É—in. Sauko wata kenan daga sama yunwa ta dame ni dan wunin ranar yau bansa komai a ciki na ba, na shige kitchen nashiga bude buÉ—e ko zan ga abin da zan sawa cikina, wani kula na buÉ—e mai É—auke da tuwon farar shinkafa mai É—ume, na É—au plt na saka laida É—aya, kana na buÉ—e É—aya kular dana gani a kusa dashi, miyar agushi ne daya ji busashshen kifi da hanta na zuba akai kana nafito parlour na zauna nasoma ciki. knocking É—in kofa akayi har sau uku akai-akai, ido naÉ—a zubawa kofar da tunanin mai buka kofar da daddaren nan, nai tunanin ko su Talatu ne, na mike a sannu na isa jikin kofar na murza key É—in tare da buÉ—o kofar. da É—an mamaki na kalli waÉ—an da ke bakin kofar, Rasheedat ta saki murmushi da faÉ—in "Kada ace bacci kike muka taso ki?." murmushin yake namayar mata ganin yanda take ta yimin magana cikin fara'a. shiko na tsaye bai yi magana ba amma idanunsa a kaina, ganin yan da ya kafe ni da mayatattun idanun nan nasa sai na saki kofar najuya na koma ciki. suka biyo bayana, zama sukayi kan kujera in da nikuma na zauna kan hannun kujerar da ke can karshe ina zaman jiran jin abin da ya kawo su da daddaren nan. Rasheedat ta dube ni fuska É—auke da annuri tace "Narako sa ne da kaina na baki hakurin rashin zuwan sa da wuri wlh ba'i ne sukayi yawa sai a hankali, gashi nan na kawo miki shi da fatan za'a kula da shi yanda ya kamata, to ni bari naje dare yana daÉ—e yi sai da safen ku Allah ya tashe mu lafiya." ta mike tare da duban Ahmad tace "Aboki bani makullin motar na koma." ido ya waro yace "A daren nan zaki fita ke kaÉ—ai? bazai yuwu ba bari nasa a maida ki." murmushi tayi tana karÉ“ar key É—in a hannun sa tace "Babu abin da zai faru da yardar Allah Allah zai tsare, ka mai da ni karamar yarin yace nifa yanzu na girma." ta kashe masa ido tana kokarin juyawa ta tafi. nayi saurin mikewa tare da dakatar da ita ta hanyar faÉ—in "Da kin tsaya kin koma da shi da zai fi muku." ina kaiwa nan na juya na haye sama... Rasheedat tayi murmushi tare da dafa kafaÉ—an sa tace "Aboki katashi ka bita ka shawo kanta, kasan amarya sai da lallami." kai ya jinjina yaruko hannayen ta duka biyu yayi kiss É—in su, kana ya lumshe idanun sa tare da buÉ—e su a lokaci guda, ya mike tsaye yace "Muje a maida ki gida hankali na zaifi kwanciya." koda suka fita É—aya daga cikin security gidan ya umurce sa daya mai da ita gida, yana tsaye saida yaga fitar su kafin ya koma ciki. yana shiga ya rufe kofar side É—in kana ya haura sama. yana kusa kansa cikin parlour'n sama, idanunsa ya lumshe tare da jan numfashi ya shaki daddaÉ—an kamshi mai sanyi da rasa zuciya, a hankali ya buÉ—e idon nasa cikin kayataccen parlour'n a fili ya furta "Masha Allah." a sannu yafara taka kafafun sa cikin parlour'n yayin da yake rarraba idanunsa ga kofofin bedroom's É—in da ke cikin parlour'n, a sannu ya nufi wasu kofafin bedroom's guda biyu wan da suke a jere, yasaka hannun sa jikin É—aya kofar ya murÉ—a a hankali ya tura kofar, ya kusa kansa ciki. can ya hangi su Naseem kan gado suna baccin su cikin kwanciyar hankali, murmushi ya sake a hankali ya karasa shiga cikin É—akin a bakin gado ya zauna yashafi gefen fuskar ko wannen su yana binsu da murmushi kamar waÉ—an da idanun su biya, kana ya mike ya daÉ—a jan bargo ya rufe musu jiki, yafita ya ja musu kofar. numfashi ya sauke lokacin da yamaso jikin É—aya kofar da ke kusa da bedroom É—in su ya tura kofar ya leko kansa ciki, babu kowa cikin É—akin sai dai a gyare yake tsaf-tsaf gadon cikin É—akin yasha shinfi É—akin sai kamshi yake tashi, shakar kamshin yayi yana mai jin daÉ—in kalar kamshin da side É—in gaba É—aya yakeyi, kuma ko wani bedroom da kalar kamshin da yake tashi. mai da kofar yayi ya rufe ya juyo ya zuba wa É—aya kofar dake can gefe ita kaÉ—ai ido. a sannu ya taka izuwa jikin kofar, sai kuma ya ja ya tsaya na Æ´an dakiku kana a hankali ya kai hannun sa jikin handle É—in kofar a hankali ya murÉ—a ya tura kofar a sannu ya kusa kansa ciki. wani irin dogon numfashi yaja yana mai shakar daddaÉ—an kamshin daya bigi hancin sa... firgit na mike zaune jin an turo kofa, cike da mamaki nake kallon sa yana tsaye idanun sa a lumshe a sannu yaware idanun nasa a kaina. A hankali ya soma takowa cikin É—akin, ina ganin haka na yi saurin zamowa bakin gadon ina binsa da kallon tuhuma, gani ya dumfaroni gadan-gadan yasani mikewa da sauri nace "Meya kawo ka cikin É—aki na?, ka ketare tun daga kasa ka hauro sama kashigo min har cikin É—aki?." sai da ya matso daf dani kafin yasoma magana "Hurimi iko mallaki, duk na haÉ—a yau, babu wani shamaki sakani na da ke meye nayi min wannan tambayar kyakkyawa ta." yayi maganar yana kokarin ruko hannuna, nayi baya da sauri cikin É—an É—aga murya nace "Kafita min a É—aki Malam." ido ya zuba min babu ko kakkauta wa yana bin jikina dawani irin kallo, da sauri na kalli jikina, riga da wando na bacci ne a jikina rigar mai tsiririn hannu irin mai gidan bra É—in nan, mai tsamtsi ne sosai ya bi jikina ya lafe. kan na an kara har ya matso daf dani har jikin mu na gogan juna, baya nayi da sauri na matsa baya kasan cewar ina tsaye daf da bakin godo ne sai ji na nayi na zube kan gadon. da sauri na mike zumbur na saka hannaye na bibbiyu na ture kirjin sa na bi gafen sa nasa kai zan wuce, sai ji nayi ya cafko hannuna ya janyo ni jikin sa har sai da na garu da jikin sa, "Ka sake ni idan ba haka ba wlh sai nayi maka abin da baka taÉ“a tunani ba." É—an rankwafowa yayi saitin fuskata a hankali ya furta "Za ki sa a zo a fitar dani ko? wani sam bazai iya ba kin taÉ“a ganin in da aka fidda miki É—akin matar sa." sai kuma ya saki murmushi mai sauti a sannu ya sauke yatsar sa kan baki na yana É—an zagaye lip É—ina, sai ya lumshe idanun sa a lokaci guda ya buÉ—e yace "Suna da kyau sosai gwanin ban sha'awa." yayi maganar tare da É—an matsa laɓɓana, da sauri na bige hannun sa, ina wasa masa harara. na fizge jikina da sauri na nufi kofa na buÉ—e nafita, É—akin su Nasmah na shige na maida kofar na rufe tare da murza key, nahaye tsakiyar su nayi kwanciya ta. A É“angaren Ahmad kuwa bayan ta yabi da kallo har ta fita, kana ya sauke numfashi a sannu ya masa bakin gadon ya zauna yakai tsawon minti 20 kafin ya mike yafita a É—akin, kasa ya sauka ya É—au jakar kayan sa ya dawo dakin, yabuÉ—e jakar ya ciro jallabiya mara nauyi ya tuÉ“e kayan kijin sa ya saka sannan ya haye gadon ya kwanta tare da janyo pillow ya rungume a jikin sa yana mai shakar daddaÉ—an kamshin dake tashi daga jikin pillow'n zuwa gadon gaba É—aya a fili ya furta "Yarin yar akwai son kamshi." sai kuma yasaki murmushi yana daÉ—a rungumar pillow'n, ya É“ata tsawon lokuta masu tsawo kafin bacci yasami nasarar É—aukar sa. Washegari kiran sallar asuba a kunnen sa ya mike yashiga bayi yayi al'wala yafito da É—an sauri ya fita dan lokacin ana kokarin tada ikama, har zai wuce yadawo kofar su Naseem ya bubbuga, kamar a mafarkk najiyo buga kofar da ake na mirgina cikin magagin bacci na É—an É—aga murya nace "Waye?." yace "Kitashi kiyi sallah lokacin salla yayi." tsaki naja jin muryar sa dan ni nagama mance wa ma da wani cikin gidan, najuya na gyara kwanciyata na mai da kaina na cigaba da bacci na, dan ina fashin sallah... Bayan an idar da salla Ahmad ya iso gurin Bappa dake zaune sakiyar masallacin yana koyawa masu aiki da security karatu, shima yaÉ—au Kur'ani akaci gaba da yi da shi, sai da guri yayi haske sosai kafin Bappa ya tashe su, kowa yafita zuwa gurin aikin sa. Ahmad ya gyara zaman sa yashiga gai da Bappa ya amsa kicin kula da sakin fuska sannan ya É—aura da faÉ—in "Ashe dai anan ka kwana." kai Ahmad ya sunkuyar yace "Eh." Bappa yace "Masha Allah to ya cikin gidan?." yace "Lafiya lau alhmdllh." É—an shiru Ahmad yayi kansa a kasa, Bappa ko farin ciki ne fal cikin zuciyarsa da yau HAMDAH ta kasance matar aure yana da tabbacin daÉ—a samin nutsuwa cikin rayuwar ta, kuma yana hasashe da sa ran mijin datake aure bazai hofantar da ita ba. Ahmad yaÉ—an muskuta har lau kansa a kasa yace "Da jiya naso mutafi can gida na da ita amma sai nayi tunanin hakan ba mai yiwuwa bane." Bappa yace "Gaskiya kam yiwuwar hakan abune mai wuya dan nasan HAMDAH bazata yarda ba, sai dai kawai karika zuwa nan É—in, a hankali idan ka shawo kanta sai ku koma can É—in." kai ya jinjina shi kansa yasan hakan shiya sa ma bai fara tinkatar ta da wannan batun ba. ganin yayi shiru bai kuma cewa komai ba sai duba agogo yake, yasa Bappa cemasa ya tashi yaje dan ya fuskanci nauyin sa yake ji. Bappa ya daÉ—a jinjina girman soyayya da aure, duba da babban mutum kamar Ahmad Tijja Sabil dayafi karfin komai sai gashi yana rusunar da kai da kuma girman sa akan mace. A hankali nayi mika tare da yin salati na mike zaune ina mussuke ido, kallon gefe da gefe na nayi, su Naseem sai sharar baccin su suke. a hankali na zamo bakin gadon na mike nashiga bayi, wanka nayi sosai kana na janyo towel daga cikin towel É—in wankan su, buÉ—e towel É—in nayi ina binsa da kallo, bashida wani girma sosai kuma a hakan duk shine babba cikin sauran towel É—in da suke jere a ma ajin su cikin bayin. a haka na É—aura bai karasa kai min guiwa ba rabin cinyata a buÉ—e yake, nafito najima tsaye cikin É—akin na rasa ta yanda zanyi na fita a haka, gashi ina jin alaman jini na kokarin sauko min, da sauri na nufi kofa ina jan tsaki dan bani da yadda zanyi pat É—ina na bedroom É—ina. a bakin kofa na tsaya ina, shiru banji alamun motsi ba, a hankali na tura kofar sai da na leka kaina ciki babu kowa cikin É—akin, a hankali nasa kai nashiga gaban wardrobe na isa na buÉ—e, pant da pat na fara cirowa ina kokarin kwance towel É—in, naji karar buÉ—e kofar bayi da sauri na mai da toewl É—in na É—aura, da É—an sauri na shiga ciro kaya na na juya zan wuce sai ganin sa nayi daf da ni, kaucewa nayi kokarin yi yataro ni da sauri ya janyo ni na fado jikin sa. "Meye haka!?." nafaÉ—a da karfi ina ture sa. a hankali yacusa fuskarsa a gefen wuya na tare da shinshinar fatar wuya na yaja numfashi, da sauri na shiga ture kansa tare da faÉ—in "Wai meye haka ne kam dalla ka kyale ni." yaciro fuskar sa sai ya sakalo hannayen sa a kuguna yace "Tun É—azu nake cikin bathroom nakasa yin wanka ban iya yi ni kaÉ—an ba sai an taya ni, muje ki tayani kinjin kyakkyawa ta.' É“ata fuska nayi nace "Nice zan taya ka wanka? capÉ—i lallai bazaka yi ba, zaifi maka kayi gaggawar zuwa in da aka saba taya kan, sake ni malam." nakarasa Maganar da buge hannunsa na juya da sauri sai ji nayi ya.......! Mommyn Twins ce 8/19/22, 10:56 - Ummi Tandama😇: *HMDH* *WASA FARIN GIRKI* *NA* *RASHEEDAT S DIRECTOR 19 Washegari da safe bayan sun karya tace masa ya tafi, yace ba yanzu ba duk yan da taso yatafi da safen yaki sai da dare yayi bayan sallar isha kafin ya tafi. Ina zaune a parlour sai ganin sa nayi, fuska na haÉ—e dan sam banso ya kuma zuwa ba,da baya gidan naji sakat na kwana É—ayan nan yazo ya takura min ya hana ni sakat nida gida na. fuskarsa É—auke da murmushi kamar kullum ya karaso, daf dani ya zauna har muna gogan juna, É—an rankwafowa yayi jikina har ina iya jiyo sautin fitar numfashin sa, ya ruko hannaye na duka biyu a sannu yashiga murza su cikin tafin hannun sa, ido yalumshi tare da buÉ—e wa sannan yace "Kyakkyawa ta babu ko É—an barka da zuwa." gajeren tsaki na ja ina yunkurin mike wa, sai yayi saurin sake hannuna yasaka hannayen sa duka ya zagaye ni ta baya, ya janyo ni ya daÉ—a mannani da jikin sa sosai, a sannu ya kawo fuskar sa daf da nawa ya haÉ—e goshina da nasa, yayin da numfashin mu ke garwaya dana juna, É—ina a hankali ya manna bakin sa kan lip É—i na yayi kissing nashi, kokarin tura harshen sa yake cikin bakina da sauri nakawar da kaina gefe. numfashi mai karfi ya sauke tare da rumtse idanunsa da karfi yakuma buÉ—e wa, daÉ—a rungumoni sosai yayi a jikin sa kana cikin kasa da murya da tausasa shi yace "Please HAMDAH ko sau É—aya kibani dama kin san yan da nake ji a kan ki kuwa?, ki taimake ni son ki na shirin illatar da ni." "Ka sake ni ni ka sake ni nace." nafaÉ—a cikin É—an gaÉ—a murya ina kokarin kwatar kaina. bai sake ni ba sai idon daya kafe ni da shi kamar zai cinye ni, niko narika mutsu-mutsu da tutture shi ina cigaba da faÉ—in "Ka rabu da ni dalla Malam ka sake ni bana so." bai ce kamai ba sai idon daya cigaba da bina da shi zuwa can a hankali yasoma magana "HAMDAH me yasa bazaki saurareni ba, baki yarda da gaske ina son ki bane ban shigo rayuwar ki dan na cutar da ke ba, son da nake miki shi yakawo ni cikin rayuwar ki, meyasa bakya sona mene ne aibu na?." Da karfi na daddage narika ture shi ina faÉ—in "Ka rabu da ni ka kyale ni bana son ka kaima zai fi maka ka daina so na." daga saman step muryar su Naseem ke tashi yayin da suke saukowa da gudu suna faÉ—in "Mommy kijo ki canja mana kallon ansa me dodo ne." da sauri ya sake ni ganin yaran suna daf da sauko wa, suka karaso da gudu suka zube a jikinsa, da sauri na mike ina wasa masa harara haÉ—e da murguÉ—a masa baki, murmushin nan nasa ya bini da shi sannan cikin É—an É—aga sauti kaÉ—an yace "Kyakkyawa ta ina son ki son ki a nan É—ina yake yakuma haifu a sassan jikina, in da duk gilmawar da jinan jikina zai yi dake yake numfasawa." ya nuna dai-dai sai saitin zuciyarsa sannan ya cigaba da faÉ—in "Bazai fita ba baku ma zan taÉ“a dai na sonki ba, kema kuma zaki soni." muryar Naseem na sinkayo yana faÉ—in "Daddy muma kana son mu?." dariya yayi yana rungume su a jikin sa yace "Kwarai ma kuwa ina son ku, kuma son ku anan É—ina yake da ilahirin jikina gaba É—aya." yanuna ka san zuciyarsa kasa da inda yace anan nake. murna suka shiga yi suna faÉ—in "Yee muma Daddy yana son mu." tsaki naja najuya na nufi sama,na barsu nan zaune suna ta tikar dariya har da shi. dogon tsaki naja ina haurawa step's "Mutum kamar mara zuciya duk abin da zaka masa bazai taÉ“a jin haushi ba, kullum fuska É—auke da murmushi kamar gonar auduga." nakuma jan gajeren tsaki ina shigewa parlour'n sama... Da daddare bayan sallar isha nafito daga bedroom É—ina bayan na sarkake jikina nayi wanka tare da É—auro al'wala dan yau nagama period, sallaya na shinfiÉ—a na gabatar da sallar isha ina idanrwa na mike naje na saka kaya, ina kokarin fita a É—akin ya shigo ganin yana kokarin matsoni,na É“ata fuska tare da kaucewa nayi waje abina. É—akin da tun ranar da yazo na dawo kwana ciki, nashige nayi kwanciya ta ci ki. sai da nagama danne-dannen wayata nakai wajen karfe 11 kafin bacci ya É—auke ni... can cikin bacci narikajin ana tattaÉ“a ni firget na mike zaune, ina ware idanuna, ni dana kwanta da haske sai na tsince ni cikin duhu yanzu, hannun mutum naji yakuma mai dawa jikina yana daÉ—a laluma ni ai da sauri nashiga lalumo wayata, ina É—auka nayi saurin danna shi ya bada haske, ai da sauri na duro a gadon nayi saurin kunna wutan cikin É—akin. yana zaune a sakiyar gadon yayin da yake ta jan numfashi da kyar cike da alamun zurfafa cikin matukar bukatuwa, zamowa yayi bakin gadon ya mike yana yunkurin maso ni da sauri na É—aga masa hannu nashiga ja da baya ina faÉ—in "Me ya kuma kawo ka nan? kafita nace ka fita!." Na karasa maganar cikin É—an É—aga sauti ina kuma yi masa nuni da kofa kan ya fita. numfashi ya ja a wahalalce yace "Kar kiyi min haka HAMDAH kar ki mance nifa mijinki ne ina da hakki a kanki, HAMDAH son ki da bukatar ki zasu iya yi min illa ki taimaka ko sau É—aya ne ki bani dama." da sauri na katse shi da faÉ—in "Ban san wannan ba kafita kawai kar kasake ka matso ni." "HAMDAH ki saurare ni." "Babu abin da zanji daga gare ka fita kawai." Kan sa ya dafe da hannaye sa duka biyu yana mai rumtse idanunsa da karfi, a hankali ya juya cikin jan kafa yafita a É—akin. numfashi na sauke da sauri na isa jikin kofa narufe kofar tare da murza key, na dawo na kwanta, nakai tsawon lokaci kafin bacci yakuma É—auka ta. washegari bayan tafiyarsu Nasmah School ina yin breakfast na tafi sashin su Inna Wuro dan sam bana so na kasance inuwa É—aya da shi. a parlour na tadda su Inna Wuro da Bappa na zauna muka ta hira, daga baya Bappa ya juya hirar izuwa nasiha, ya mai da hankalin sa sosai a kaina tare da kiran sunana ya cigaba da faÉ—in "HAMDAH cikin gidan naku lafiya dai ko?." kai na gyaÉ—a da faÉ—in "Lafiya lau Bappa." yace "Masha Allah Allah ya daÉ—a dauwamar mana lafiya da kwanciyar hankali, to HAMDAH yanzu Allah ya kawo ki wani lokaci na musamman sai kin jajirce wajen gudanar da lamarin ki, Allah ya É—aura miki wani nauyin da dole sai kin bada kulawa sosai wajen isarwa da kuma sauke wa, kiyi kokarin sauke duk wani nauyi da hakkin daya rataya a wuyan ki, ta nan ne kaÉ—ai zaki da É—a ganin falala da ci gaban rayuwa, HAMDAH mijin ki yana da hakki mai girma a kan ki, kiyi kokari ki jajirce wajen sauke duk wani nauyin daya rataya a kanki, ki guji duk abin da zai kaiki da halaka, miji yana da hakki mai girma a kan matar sa kamar yadda itama take da hakki a kansa, amma ki sani aljannar mace yana karkashin kafar mijin ta ne, idan tayi masa biyayya ta sauke dukkan hakkokin sa, to babu makawa da yardar Allah zata shiga aljanna cikin sauki. idan kuma ta bijire masa to tana cikin asara, kiji tsoron Allah aduk inda kike kizamo mace ta gari in da zakiji daÉ—i ranar gobe kiyama, aure ba abin wasa bane darajar sa yawuci duk in da ake tunani, idan kayi wasa da shi ko ka nimi ka wulakanta shi ko ka É—auke shi abin banza, hakika zaka ga rashin daidai a rayuwar ka tun anan duniya, yan da idan kayi biyayya ka tsare dokokin sa zai kaika ga aljanna, haka zalika idan ka hofantar da shi zai jaka izuwa wuta, Allah ya tsare mu da yin abin da zai kaimu ga shiga wuta." Inna Wuro ta amsa da "Amen ameen ameeeeeen ya rabbil izzati." Bappa yaci gaba da yi min nasiha mai matukar shiga jiki da tsoratar wa, ba shakka jikina yayi sanyi zuciya ta ta kariya, lallai duk kan musulmi mai imani babu wanda zai so ganin sa cikin azabar Ubangiji. muna nan zaune Bappa bai gushe wajen cigaba da yimin nasiha ba. har Ahmad ya shigo shima ya zauna Bappa yaci gaba da yi mana nasihar tare, babu wariya ko nuna banbanci... Bappa ya É—au tsawon lokaci yana yi mana nasiha daga bisani ya rufe taron da addu'a. Ahmad yayi ta masa godiya kana ya tashi ya fita. fitar sa bada jimawa ba, Inna Wuro ta dube ni tace natashi naje ko zai bukaci wani abu ni ina nan, na mike jiki asanyaye tare da yiwa Bappa godiya natafi.. A parlour'n sama na tadda shi yana zaune yana waya, na wuce shi na shiga bedroom É—in dana koma kwana ciki, na kwanta bakin dago jiki ba kwari dan gaba É—aya jikina yagama mutuwa da wa'azin Bappa, shiga ta bada jimawa ba ya shigo, har ya karso in da nake ban É—ago ba, ya tsaya ta gurin kafafu na "Bacci zakiyi ne?." yayi maganar idanunsa a kaina, tsintar kaina nayi da gyaÉ—a masa kai. kai ya jinjina yace "Kiyi bacci mai daÉ—i ni zan fita akwai waÉ—an da suke jira na zamu yi zama, sai na dawo." nan ma kai na gyaÉ—a ma sa, ya juya yafita da murmushi. ina dai kwance badan bacci ya É—auke ni ba har su Nasmah suka dawo daga school.. shiko tun da yafita bai dawo ba sai daf magriba, yana shiga kuma ya ja Naseem sukayi masallaci. sai bayan sallar isha suka dawo.. Tun daga rana mai kamar ta jiya Ahmad bai sake tinkara ta da bukatar sa ba, yakuma dai na yunkurin taÉ“a jiki na, zai dai zauna a inda nake yayi ta jana da hira haÉ—e da wasa, tun ina yin banza da shi har yakai ga nakanyi murmushi da jin wani zancen nasa. Yau kimananin satinsa biyu kenan a gidan,duk bayan kwana biyu yakan cemin zaije ya duba Kawa, idan kuma ya dawo zai zo min da sakon cewa tana gaishe ni. Zaune na ke a É—aki ina jiyo muryar su a parlour shi da su Naseem kasan cewar yau weekend ne, shima babu in da ya je har yanzu wajen karfe 12 da rabi, a hankali na mike jin an fara kiraye-kirayen sallar azahar, nashiga bayi nayi al'wala na fito, Nasmah ce ta shigo tace "Mommy Daddy sun tafi masallaci yace nayi salla na a gida zan sami lada da yawa da yawa kamar haka." ta kwatanta da faÉ—in hannayen ta biyu, murmushi nayi nace "To je kiyi al'walar kizo muyi sallah." tawuce da sauri tayo al'walar tafito mukayi sallar tare. muna idar wa tayi waje dagudu wai zataje ta duba ko su Daddy sun dawo.. na mike na ninke sallayar na kaisa ma'ajin sa, kana na koma na kwanta... turo kofa yayi da salla na amsa batare da na É—ago ba, ya karso cikin É—akin abakin gadon kusa da kafafu na ya zauna, a sannu ya É—ago kafafuna duka biyu ya É—aura kan cinyar sa, a hankali yashiga matse su yana É—an jajjan yatsun tare da É—an tankwashe su yana cigaba da matse su a hankali. Idanuna na lumshe tare da buÉ—e su batare da na yi yunkurin hanasa abin da yake yin ba. É—an tsuramin ido yayi a hankali yace "Tun jiya Hajiyar mu take ta tambaya ta ke wai bazan kawo ki ki gaishe ta bane, ko yanzu tafiya ta masallaci ma sai da ta kuma kira na, ya kama muje ki gaishe ta, ko bacci kike ji abari sai kin tashi?." kamar nace Eh amma jin ya ambaci Hajiyar mu nasan cewa mamansa ke nan yake nufi, uwa kuwa ta wuci wasa dan kullum da nawa uwar nake kwana nake tashi, kai na girgiza masa alamun ba baccin nakeji ko zanyi ba. yace "Okay to ki shirya muje a gaishe ta." nan ne dai ban amsa sa ba ya É—aga kafafu na a hankali ya aje su kan katifa kana ya mike yafita. a sannu na mike na sauko a gadon bayi na shiga nayi wanka batare da É“ata lokaci ba na fito, na zauna gaban mirror mai da pauda da man lip kaÉ—ai na goga, na mike na isa gaban wardrobe É—in É—akin naciro doguwar riga daga cikin kayana dana kawo su É—akin, haÉ—e da bra da pant da sket Æ´ar ciki. ina gama sa kayan nazo gaban mirror nayi rolling É—in gyalen doguwar rigan a kaina, na fesa turare mara karfin kamshi sosai na É—au wayata haÉ—e da hand bag, nasa takalmi mai É—an tsini ba can sosai ba nafito, jin babu motsin kowa a parlour sai na nufi kasa, tun daga saman step's ya kafe ni da ido, a hankali nake É—aga kafata sabo da takalmin dake kafata gudun tsamtsin step É—in. a hankali na sauko, nan na tadda su Nasmah cikin sabuwar shiga da alama wanka a ka sake musu. kai na na kawar gefe ganin yan da yake bina da kallo babu ko kifta ido, lallausar murmushi ya sake yace "Kyakkyawa ta kinyi kyau sosai." baki na taÉ“e ina mai cigaba da kawar da fuskata. yamike ya ruko hannun su Naseem yana faÉ—in "Ku taso muje ko, kada Madam ta gaji da tsayuwa." suka nufi kofa nabiyo bayan su, muna isa gurin motar da É—an sauri yadawo gefen mai zaman banza ya buÉ—e ya dube ni sannan yace "Madam bismilla." ba tare dana kalle sa ba na shige cikin motar, yana kokarin rufe kofar nayi hanzarin kai hannuna naja kofar da kaina na rufe. murmushi yayi kana ya zaga ya buÉ—e wa su Nasmah suka shiga, sannan ya dawo gefen direba ya shiga yaja motar a hankali, mai gadi ya buÉ—e get yasa kai yafita a hankali... A hankali muka haura titi in da yake tukin kamar bazai yi ba, a bakin wani katafaren ShopRite muka tsaya, ya dube ni sannan yace "Ko zakiyi wa Hajiya tsaraba?." shiru nayi ban amsa shi ba sai kuma na buÉ—e marfin motar na fita, shima ya fito kana ya fito da yaran ya ruko hannun su muka shiga ciki, tarba na musamman aka yi mana cike da girmamawa a cikin gurin, turaruka da sabulai masu kamshi da tsada na É—iba cikin basket É—in da na É—auka, su Naseem kuwa suka rika jidar kayan zaki, shima yana taya su. nazo gurin biyan kuÉ—i sai suka karÉ“i basket É—in da sauri suka zuba kayan cikin laida, ATM nayi kokarin cirowa acikin jakata, É—aya daga cikin masu amsar kuÉ—i yace "Hajiya kibar shi." naÉ—ago jin abin da ya faÉ—a lokacin su Ahmad duka karaso gurin da sauri suka karÉ“i basket É—in hannun yaran suka juye kayan cikin laida, É—aya daga cikin ma'aikatan gurin ya karÉ“i laidodin da sauri yayi waje nan muka bi bayan sa,ban kuma ga lokacin da ya biyasu kuÉ—in su ba. acikin mota mutumin ya aje laidodin kana ya gaÉ—a hannu yana yi mana sallama, ina dai-dai ta zamata cikin motar kamar ance na É—ago idanuna ya sauka can saman katafaren ShopRite É—in, sunan sa ne manne da manyan harufa. baki na taÉ“e a raina nace "A she dai nasa ne shiya basu amshi kuÉ—in ba." a bakin get É—in wani katafaren gida yayi hon, batare da É“ata lokaci ba a ka wangale get É—in muka kusa cikin gidan, gida ne katon gaske wan da girman sa yakai ya kawo. a tsakiyar gidan ya paka motar in da mutane sukayi ta zuwa suna mika masa gaisuwa ba shi kaÉ—ai ba har da ni. har muka fita a cikin motar muka nufi ciki mutane nata tururruwan zuwa suna kwasar gaisuwa. wani katafaren parlour muka bayyana cikin sa, da salla na saka kafata ciki. wasu mata ne da Æ´ammata ke zaune cikin parlour'n, kamar bazasu amsa sallamar ba yayin da dukkan su hankalin su ke kan abin da suke, sai da É—aya daga cikin su ne ta É—ago sai kuma tace "La Ya Ahmad." sai dukan su suka É—ago suna mai amsa sallamar da faÉ—in "Sannu da zuwa." wata daga cikin su ta dubi Ahmad tana wani karairaya tace "Sannu sa zuwa Ya Ahmad." bai amsa ta ba sai sauran da suke ta faman mika masa gaisuwa ya amsa kana yace "Hajiya fa." da sauri wacce yaki amsa gaisuwar nata tace "Tana ciki bari nayi mata magana." da sauri ta wuce jim kaÉ—an ta fito tana girgiza kugu tace "Wai ka shigo." hannunsa naji cikin nawa da sauri na wai ga in da yake murmushi ya sakar min yace "Muje." a hankali muka nufi cikin wani dogon corridor kana muka isa baki wani kofa, yayi sallama bakin kofar daga cikin É—akin aka amsa yayi min alama da mushiga, na zame hannuna cikin nasa yafara shiga mukabi bayan sa.......! Mommyn Twins ce 8/19/22, 10:57 - Ummi Tandama😇: *HMDH* *WASA FARIN GIRKI* *NA* *RASHEEDAT S DIRECTOR* 21 Kallon sa nake cikin matukar tausaya wa, tabbas rayuwar sa abin a tauya ne, yana ji yana gani ake niman hallaka rayuwar sa, kuma a haka yake rayuwar sa tamkar bayi da wasa matsala, kullum fuskarsa É—auke da farin ciki kullum acikin dariya da fara'a yake, ikon Allah to shi wannan wani irin mutum ne haka?. hawaye ni naji sun zube min jikina yayi sanyi na mugun tausaya wa rayuwar sa da yake cikin hatsari. magana ya cigaba da yi "Ta nimi Rasheedat da kusan irin haka sai dai ita bata kaiga bata magani ba, kasan cewar Rasheedat a gidan mu ta tashi tasan dukkan halin ta, tun da ta fara faÉ—a mata wasu maganganun da basu É—auke ta ba, sai ta yi saurin bijire mata, shike nan tun daga ranar ta É—au ki tsana ta kuma É—aura mata, dan dama sam bata son auren mu da ita tun da naki amin cewa da auren É—iyar kanin ta, ako da yaushe cewa take wai tayi mata rashin kunya." Numfashi na sauke nakai hannu nashare É—an guntun kwallar da ya zubo min a hankali nace "Shine kake cin abincin ta baka jin tsoron ta zuba maka maganin ciki?." murmushi yayi tare da jan kumatu na yace "Kina ji min tsoro ne kyakkyawa ta?." ido na lumshe tare da kuma buÉ—e wa. numfashi yaÉ—an sauke sannan yace "Bazata taÉ“a gangancin yunkurin yin hakan ba, dan ita a karamin tunanin ta idan ta yi haka za'a iya zargin ta, shiyasa bata taÉ“a yunkurin kwatanta hakan ba, sai dai tasa ayi, kada kiji tsoron ta idan ta gane kinji tsoron barazanar da ta miki, zata kuma samin da mar cigaba da yi miki barazana, idan ta kuma tarar ki da maganar kice ta sallawantar da rayuwar naku in zata iya, zata kuma yi miki barazanar da zai firgita ki kada kiji tsoro dan babu abin da zata iya." kai na girgiza jiki a sanyaye, janyo ni jikin sa yayi tare da sakin Æ´ar karamar dariya yaleko fuskata sai ya kuma sakin murmushi mai sauti cikin yanayin sa na zolaya yace "Har yanzu wayo da saura tukun ayi maka tayin dukiya mai yawa kaki karÉ“a." baki na turo gaba tare da janye jikina daga nashi ina ai ka masa da harara, nayi yunkurin mike wa. ya mai dani jikin sa yana dariya kasa-kasa.. yana yin sa yana bani mamaki shi da yakamata yayi zaman kunci amma ko da yaushe yana cikin walwala... After 2 week Hakan yayi dai-dai da watan Ahmad guda a gidan nan, a daren jiya ya koma gidan sa, tare da su Naseem ya tafi kasan cewar daren weekend ne jiya. zuwa yanzu nakan É—an sake masa har idan ya na yimin hira nakan É—an rika amsa masa, duk sona dana rika share sa amma sai yasan hanyar da yabi yasa na kula shi, Ahmad mutun ne mai saukin kai, yana da faram-faram da son yawan fara'a da zolaya bashi da É—aure wan kai ko kaÉ—an.👌🻠Zaune nake a É—aki kiran Bappa yashigo waya ta, ko da na É—aga yace idan ba abin da nake nazo nace to. a hankali nafita, shiru parlour babu motsin kowa, daga jiya zuwa yau side É—in yadawo wani shiru haka babu hayaniyar su. na wuce sashin su Bappa bayan mun gaisa Bappa ya É—aura da faÉ—in "Jiya nasami kira daga jagororin da a ka É—aura kan kula da ma'aikatan mulmula karfe daga Lagos, abun farin ciki suke shaida min an kammala ginin yau kuma da yardar Allah jirgi zata iso da kayan aiki." baki na washe cike da farin ciki nace "Masha Allah Allah abin godiya." Bappa yace "Kwarai kuwa, yanzu in da a ce so shine samu ya ace jibi muna can a sauke kayan a gaban mu, yanzu sai ki nimi izinin zuwa a gurin mijin ki idan ya barki jibin sai mu je, gobe sai aje a biya kuÉ—in jirgi idan Allah yakai mu jibi da safe sai mu É—aga." "Izinin miji sabon salo lallai ma." nayi maganar a kasan raina maganar sa na jiyo yana faÉ—in "Idan bai barki ba kada ki matsanta ni zan tafi, duk randa Allah yasa ya bari kije sai kije daga baya." da sauri nace "Bappa sai ya bari ai dai yasan irin harkoki na kuma dan shi ai baza a fasa zuwa ba." "Akul É—in ki kada na sake jin wannan maganar yafito daga bakin ki, idan yasan harkokin ki ai da da yanzu ba É—aya bane, kuma ba'ayi yarjejeniya dashi kan zaki iya tafi gurin harkokin ki a duk sanda bukatar hakan ta taso ba, kin san girman aure kuwa? to kada ki kuskura kiyi wasa da shi, ko nan da kofar gida kika leka har idan bada izinin sa ba sai mala'ikan Allah sun tsine miki, aure ba abun wasa bane HAMDAH yazama dole ki nimi izinin sa a duk sanda fita ya kamaki, bijere wa hakan saÉ“awa dokar Allah ne, ki tambaye sa idan ya barki sai kije, kada ki kuskura ki tafi bada izinin sa ba, kinji ko?." kai na gyaÉ—a, yace "Yauwa Allah yayi albarka ki tashi kije idan ya barki sai mu tafi jibin." nace to na mike na fita, ina tafiya ina magana "Wai shi miji in za'a fita wai sai an tambaye shi." na kaÉ—a harshe tare da yin kwafa.. ina shiga side É—ina na tadda su Talatu sun shigo yin aikin su na zauna nan parlour'n kasa suna aikin muna É—an taÉ“a hira.... Washegari da yamma lis su Ahmad suka dawo, su Naseem suka yi ta cike ni da surutu da labaran abunuwan da sukayi aka kuma yi musu, cike da kewar su narika biye musu ina dariya, suka rika bani labarin wai É—ayan Mamyn su tayi musu kaza wai É—aya Mamyn su na É—aya gidan Daddyn su har goyon su take. ni dai sai binsu da dariya neke... da daddare bayan sallar isha ina zaune bakin gado Ahmad ya shigo da sallama, na É—ago na amsa masa sallamar tare da mai da kai na kan wayar dake rike a hannuna. ya karaso cikin É—akin a gefe na ya zauna, ya leko fuska ta yace "Kyakkyawa babu ko É—an barka da zuwan nan ne?." baki na cuno gaba, murmushi yayi yace "Yaushe ne zaki fara yin murna da gani na?." baki na murguÉ—a ina kokarin kawar da fuska ta yiyi saurin juyo fuskar tawa ya sauke min kyakkyawar sumba kan lip, ya É—an lumshe ido tare da buÉ—e su a kaina a hankali yace "Suna da kyau da daÉ—in tsotsa." yayi maganar da É—aura hannu kan lips É—i na, hannun sa na bige ina cuno bakin gaba. murmushi yayi mai sauti. mike wa yayi zai fita har yakai bakin kofa naÉ—an kalle sa nace "Bappa yace na faÉ—a maka zamuje Lagos jibi." nayi maganar a takaice ina janje idona daga gare shi. a hankali ya juyo daga in da yake tsaye yace "Ayya Bappa Malam Allah ya tsare masa hanya." a hatsale nace "Har da ni zamu tafi." ido yaÉ—an waro yace "Wa har da ke ina ban amince ba bazaki jeba." a hatsale na dube sa nace "Bazan je ba? ka faÉ—i son ranka kasan dai da harkokina ka same ni tafiya kuma ba bashi." murmushi yayi tare da faÉ—in "Bazaki je ba haka na ce, shi harkokin naki sai na datse su a yau, duk ranar da kikayi wayon sanin iya tambaya ta da kanki ba basai an sa ki, ki tambaye ni ba wata kila na barki kije." yana kaiwa nan ya juya yayi waje. Wani shekeke nabi bayan sa da kallo abin ya ban haushi, wai nice yau zanje wani guri nake tambayar wani har yake ikirarin cewa bazani ba. a fili nace "Idan nazo tafiya ka janyo ni na fito cikin jirgin dan kasamu ma na tambaye kan idan badun Bappa ba babu abin da zaisa na tambaye ka." naja gajeren tsaki tare dayin kwafa. washegari da safe Bappa ya kirani yace za'a je yin bukin na jirgi shin na tambaya an barni. jin nayi shiru yasa Bappa faÉ—in "Idan kin san ba'a barki ba kada ki yi gigin tafiya gashin kanki, ki hakura kawai." a hankali nace "Bappa zai bari ma." na kasha wayar da sauri na mike na fita na nufi kofar bedroom É—ina, har na É—aura hannu kan handle sai kuma na tsaya, wai wannan mutumin me yake É—aukar kansa ne na rantse sai na zana masa iyakar sa idan ba haka ba shi har wani ji yake wai shi miji ne. da karfi na murÉ—a handle É—in natura kofar da karfi, yana kwance a kan gado, yana kwance babu riga a jikin sa ya rufe jikin sa da blanket daga kafafun sa zuwa cikin sa idanunsa a lumshe da alama bacci yake, na karaso bakin gadon na tsaya tare da rike kugu. nasoma magana a hatsale cikin É—an É—aga sauti "Wai na ce zan tafi kana gwada min bazani ba a wani dalili?, kada kaga ina tambayar ka, karika son gwada min wani bushashen iko, narantse badun Bappa ya matsa min da sai na tambaye ka ba da ba abin da zai sa na tambaye ka, kuma yan zu ma tafiya ta zanyi ko ka bari ko baka bari." duk maganar da nake idanunsa a rufe hannu na mike da zummar bubbuga shi ya tashi yaji matsaya ta, sai ji nayi ya fisgoni nafa faÉ—o jikin sa, blanket É—in jikin sa ya zare, babu komai jikin sa sai boxes, kokarin yunkurawa nake sai ya janyo ni ya haÉ—e ni da jikin sa, wani irin shack naji lokacin da na jini cikin fatar jikin sa, yayin da É—umin jikin sa ya ziyar ci ilahirin jiki na. ya saka hannayen sa gaba É—aya ya zagaye ni da shi babu ta in da zanyi na kwace kaina. a hankali ya buÉ—e idanun sa ya zuba su cikin nawa, numfashi ya sauke a hankali ya soma magana "Yau she ne tafiyar naku?." da sauri nace "Gobe." yace "Allah ya kai mu kicewa Bappa na amince kuma nima zan faÉ—a masa dan kar yayi zaton kin faÉ—a ne kawai, hakan yayi miki?." a hankali cikin sanyin jiki da jin yan da ya amsa min duk da yan da nayi ta masa maganar a tsaye, sai na gyaÉ—a masa sai. murmushi ya sakar min yace "To Allah ya kaimu goben." a kasan raina na amsa da amin, idanunsa ya lumshe a hankali ya buÉ—e su, a sannu ya sauke bakin sa kan goshi na ya manna mishi kiss, a hankali ya shiga yawo da hannunsa a bayana, jin abun nasa yana kokarin zarce iyaka, sai nayi huff zan mike na kasa sai na shiga ture sa ina faÉ—in "Sake ni ka dai na bana so." yace "Ina bacci na kika zo kika tada ni, alhalin ke ba tayani baccin zakiyi ba, da kyar na samu wannan baccin ya É—au keni shine zaki É“ata min shi, to ai biya na zakiyi É—umi zaki bani zan iya komawa baccin wata kila, idan kuma ban koma ba to sai kin bani asalin É—imin, dan bazaki É“ata min bacci kitafi ba." yana karasa maganar ya zuge zip É—in riga ta har kasa ya raba shi da mahaÉ—in sa, ido na waro jin yana kokarin rabani da rigar, kafin nayi auni ya zare ta a jikina, wani irin nannauyan numfashi ya sauke, ido ya kurawa fararen nonuwa na da suke cikin bra, numfashi ya fizga da kyar, da sauri ya haÉ—e kirji na da nashi tsam ya rungume ni. niko turesa na cigaba da yi ina fadin ya sake ni, bai kula ni sai da muka kai tsawon minti 20 a haka, kafin yashiga sassauta min rukon da yayi min, yayin da gudun numfashin sa yakaru. da sauri na janje jikina na duro a gadon ban ko tsaya É—aukar rigata ba nayi waje, sai da na koma É—aya É—akin kafin na sauya kaya.... Washegari da misalin karfe 9 muka fito parking lot, Inna Wuro da ma'aikatan gidan suna ta yi mana Allah ya tsare, Ahmad da Bappa tuni sun shige cikin mota dan shi zai kaimu airport na isa jikin motar na buÉ—e gefen mai zaman banza na shiga, yaja motar suna É—aga mana hannu muka fita, dashi da Bappa sunata hira yayin da yake ta bina da kallon kasan ido, baki na murgaÉ—a masa na kawar da kaina. har muka isa airport bai fasa bina da kallon ba. yana dai-dai parking Bappa ya fita ina kokarin buÉ—e motar naji hannun sa kan cinya ta, yashiga murza shi da sauri na juyo muka haÉ—a ido, a hankali yace "Zanyi missing É—in ki." kai kawai na kawar na buÉ—e motar na fita. bai bar airport É—in ba sai da jirgin mu ya tashi.. ko da ya koma gida jiran lokacin tashin su Nasmah yayi daga school lokaci nayi yaje ya É—auko su yawuce da su can gidan sa... Ranar da muka isa Lagos washegari aka shiga da kayan aiki cikin katafaren Company, aka shirya komai a ma'ajin sa, aka rufe Company sai an É—ibi ma'aikata kafin ayi bikin buÉ—e Company. Kwanan mu uku a Lagos muka juya Abuja. ko da muka iso nayi mamakin ganin sa a airport ya kwashe mu yayi da mu gida. muna isa gida baccin gajiya na kwanta dan tun da muka tafi ban sami nayi baccin kirki ba. sai yamma lis na farka, na faÉ—a bayi nayi wanka nafito naci abincin da naga an shirya saman dinning, nayi ta zuba idon gani su Naseem sun shigo shiru, na mike na sauka kasa Talatu na tarar a kitchen tana gani na ta kara yimin gaisuwar yaya gajiya, na amsa nace "Su Naseem fa basu dawo bane?." tace "Eh gaskiya ban gansu ba naga Alhaji ya shigo amma ban da su ina ga bai dawo da su bane." ban kuma cewa komai ba na juya na koma sama, zuwa yanzu kam ina so na gansu duk da kullum sai munyi waya da su ta wayar Ahmad a rana fin sau biyar. bayan sallar isha ina idar da sallar na shiga bayi wanka na kuma nafito É—aure da towel, turus na ja natsaya ganinsa zaune a bakin gado, fuska na É“ata na karaso cikin É—akin ina É—an jajjan towel É—in kasa dan rabin cinya ta ya tsaya. ido ya zuba min babu ko kiftawa. tsayuwa nayi a tsakiyar É—akin na É—an dube sa nace "Ka fita zan sa kaya." ido yakanne yace "Æoye min halal É—i na za'ayi, to shike nan bari na rufa idanuna kisa kayan ki." ya kai hannunsa duka biyu ya rufe fuskarsa yana faÉ—in "Narufe kisaka." É—an guntun tsaki naja na isa in da hijabin salla na yake na É—auka ina kokarin saka sai ji naya an fizge, da sauri na waigo nace "Meye haka? ka bani hijabi nasa." cilla hijabin gefe yayi yadaÉ—a matsowa daf dani sosai har muna gogan juna, a hankali ya sauke hannunsa kan kafaÉ—a ta yashiga murza shi a hankali, yace "Me yasa zaki cigaba da sanya masa hijabi a sakanin mu, kyakkyawa ta bakya tausayi na ne? a koda yaushe zaman jiran ranar da zaki juyo gare ni nake, sam bana so nayi miki dole, har yaushe zamucigaba da irin wannan zamar, kin san daya nake iya bacci da ciwon sonki da bukatar ki, shin kin mance ina da hakki a kanki ne, bakya tsoron Allah ya tambaye ki kan hakki na?." da sauri na kai hannuna kan nashi jin yana gangaro da hannun izuwa saman kirji na, na janye hannun shi ina faÉ—in "Wani hakkin ban san shi ba." murmushi ya sake yace "Dagaske to bari na nuna miki." cak ya É—ago ni yadire ni kan gado shima ya hau ido na rumtse da karfi jin ya sauke hannunsa kan kirji na yana kokarin kwance towel É—in da ke jiki na. da karfi na rirrike hannunsa nace "Kada ka kunce na rantse idan ka kunce..." cak na haÉ—iya ragowar maganar tawa jin ya..........! Mommyn Twins ce 8/19/22, 10:57 - Ummi Tandama😇: *HMDH* *WASA FARIN GIRKI* *NA* *RASHEEDAT S DIRECTOR* 20 Nayi sallama ina kusa kaina cikin É—akin, wata Æ´ar dattiju war mata ce ke hakimce a kan kujera, ta amsa sallamar tana mai faÉ—aÉ—a fuskarta da murmushi, tace "A'a manyan ba'ki ne agidan namu? barkan ku dai sannu ku da zuwa,zo zauna nan É—iya ta zo maza ki zauna a kusa da ni." ta nuna min gefen kujerar da take kai na alfarma. a hankali na karaso ina kokarin zama a kasa gefen kafafun ta tace "A'a tashi ki zauna a sama." kai na sunkuyar cike da jin kunyar cewa na zauna a sama in da take zaune sai na gyara zamata a kasa gefen kafafun ta ina mai cigaba da tsunkuyar da kai. a sakiyar É—akin ya zauna kan lafiyayyen carpet mai laushi da É—aukar ido, in da su Naseem suka zauna a gefen sa. a hankali cikin sunkuyar da kai nace "Inayini Hajiya mun same ku lafiya." fuskata ta leko tana faÉ—in "Lafiya lau amarya kunzo lafiya?, wato Ahmad sai yau yakawo min ke ko, ai ko Allah yayi albarka ace rayuwa tana yin dai-dai." kai na daÉ—a sunkuyar wa ina wasa da Æ´an yatsu na ina murmushi. shima ya gaishe ta ta amsa tana mikawa su Nasmah hannu tace "WaÉ—an nan kyawawan yaran sune jiko kin nawa kuzo kusa da ni, kai ma Allah ya nuna min ranar da zanga naka haka tafe da kafar su." murmushi yayi yana amsawa da amin Naseem ne kaÉ—ai yaje gurin ta Nasmah kam kin zuwa tayi sai daÉ—a lafewa jikin sa tayi... nan da nan ta saka aka cike mu da kayan ci da sha, ta dube ni cikin kula tace "Ban ga kinci wani abin kirki ba, ko da wani abin da kike bukata ne daban akaso miki?." kai na girgiza nace "A'a waÉ—an nan ma sun isa nakoshi ne." baki ta washe tace "To madalla ai koshi shi mukafi so, ka shigo gida kamar wannan kafita bada koshi ba ai shigar batayi amfani ba." murmushi nayi ina cigaba da wasa da yatsun hannuna. murmushi yayi yana yimin kallon kasa-kasa. hira sosai Hajiya tayi ta jana da shi har na É—an fara sake wa can ya mike yana duba agogon dake É—aure a hannunsa yace "To Hajiya zamu koma." da sauri tace "A'a tun yanzu? na É—auka sai dare ai ku koma." yace "Yaran suna da islamiyya ne ga lokacin zuwan su yayi sai ranar da babu makaranta zasu zo su wuni miki." tace "Amma kam banji daÉ—i ba ace yanzu kuzo yanzu ku koma, to in za'a sake kawo min su a kawo su da wuri su wuni min." yace "To insha Allah." tace "Allah ya tsare min kai gaban ka da bayan ka yarabaka da sharrin makiya ya bada Sa'a." "Amin amin." ya amsa da shi fuska É—auke da murmushi yana kuma yi mata godiya, Ummi na ne ta faÉ—o min "Hakika lallai uwa akwai daÉ—i Ummi na kiyi ta bina da addu'ar ki nasan a koda yaushe shi ke sani nutsuwa." kayan tsarabar da nayi mata na ajiye mata tayi ta godiya nan ta karÉ“i number ta mukayi sallama, har kofan parlour ta rako mu tana É—aga mana hannu. muna isa gida kiran Hajiya na shigo wayata tayi min sannu da hanya nayi mata godiya. Talatu tayi wa su Naseem shirin islamiyya suka tada daru su sam Daddy'n su ne zai kaisu ba direba ba, haka ya É—ibe su a mota ya kaisu makarantar, ko da lokacin tashi yayi ma shi yaje ya É—auko su.... da daddare ina kwance har bacci yafara É—auka ta naji karar wayata, na É—au wayar ganin mai kiran nawa sai na É—aga da É—an sauri nakai wayar kunne tare da yin sallama. daga cikin wayar Hajiya tace "HAMDAH kuna lafiya kada ace dai na tashe ki a bacci?." murmushi nayi nace "A'a babu komai wlh lafiyar mu kalau." tace "To madalla a gaida yaran." nace "To mun gode sai da safe." ina sauke wayar sai ganin mutum nayi tsaye a kaina, yaÉ—an tsura min ido sai kuma ya tsunkuyo kaina ya shafo gefen fuska ta, da sauri na ruko hannun sa nace "Kabar taÉ“a ni." ido yakuma tsura min kana ya saki murmushi a hankali kamar maiyin raÉ—a yace "Nataya ki bacci?." da sauri nace "A'a." sumbatar kumatu na yayi yami ke yana faÉ—in "Kiyi bacci mai daÉ—i sai mun haÉ—u a mafarki." baki na murguÉ—a lalkausan murmushi ya sakar min ya juya yafita tare da jamin kofa... Bayan kwana biyu yau ta kasan ce ranar asabar, da safe ina zaune a É—aki ya shigo cukin É—akin cikin shiga ta alfarma yayi kyau sosai ga annurin fuskar sa da ke abaytane mai karawa fuskarsa kyau, ya karaso ya zauna a gefe na, plt É—in da ke gabana mai É—auke da kayan fruit mai sanyi ya kai hannu ya É—au fork É—in da nake ci da shi ya É—iba ya kai bakin sa, ido ya numshe yana taunar sa sai kuma ya buÉ—e idon a kaina yace "Kice kayan daÉ—i kike ci shine kika É“oye a É—aki kika barmu can parlour Babu ko É—an tayin nan ma." fuska na yamutsa a kasan raina nace fruit É—in ne shine kayan daÉ—in." "Kayan daÉ—i ne mana baga shi kin É“oye saboda kar muci ba." ido naÉ—an waro dan banyi zaton maganar tawa ta fito ba sai kuma na taÉ“e baki. ya É—ibo fruit É—in ya kawo shi saitin baki na yace "BuÉ—e baki na sami kyakkyawa ta." fuska na kawar ina tura baki gaba, murmushi mai sauti yayi yace "To ni saka min gashi na buÉ—e baki na." ya buÉ—e bakin wanda jerarrun fararen hakora sukayiwa kawanya ciki, harshe mai taushi yakara daÉ—a masa kyau gwanin burge wa. fuska na É“ata na kai hannu batare da na É—au fork É—in da ya ci da shi ba naÉ—au yankakken ayaba na kai bakina, zaman sa ya gyara da kyau ya janyo ni jikin sa, hannayen sa duka biyu ya saka ya tallafo kaina da kyau in da bazan iya kwatar kaina ba, da sauri na rufe idanuna ganin yana kokarin jefa fitanannun idanun sa cikin nawa, saukar lips É—in sa naji kan nawa kafin nayi wani yunkuri sai jin É—umin harshen sa nayi cikin bakina, a hankali cikin wani irin salo yake juya harshen sa cikin bakina, a sannu yashiga tsotsar ayabar haÉ—a da harshe na, wani irin fitinannen numfashi yake fiddawa da sauri da sauri ya É“ata tsawon mintu goma a haka, sai da ya tsotsi ayabar nan ta narke duka ya shanye ta. kana a hankali yazare bakin sa a tare muka saki numfashi dukan mu, baya nayi na jigina da jikin gado tare da hararan sa dan naka sa magana, shiko murmushi yayi tare da kashe min ido yana mai jan numfashi da kyar yana mammatse fitinannun idanun sa da suka sauya kala, baki na turo gaba na kawar da kaina gefe. a hankali ya shafo gefen fuskata yace "Kin wa hajiya alkawarin zaki je ranar weekend sai kirana take tun sassafe." shiru nayi ban ce komai ba, dan jiya nima ta kira ni nace mata zamuzo ranar asabar ko lahadi. yace "Sai ki tashi ki shirya ki cika alkawarin da kika yi mata muna jiran ki a kasa." ya mike tare da sumbatar goshina ya juya yayi waje. numfashi na sauke a hankali na mike na faÉ—a bathroom. cikin minti 25 nagama shiri nafito na same su a kasa, ban ko kalle sa ba duk da tulin kallon da yake ta aika min da murmushin sa mai bayyanar da ainahin kyan fuskarsa, nayi waje suka biyo ni yana faÉ—in "Ba jira ne Madam?." nam ma ban tanka shi ba. har muka shige mota yanata zolaya ta da jana da wasa wani bin, idan yayi abib dariya sai na sinci kaina da yin murmushi amma aÉ“oye bana bari ya gani. a haka muka isa gidan. Yana dai-dai ta parking ya dube ni tare da ruko hannuna ya matse cikin nashi, yaÉ—an rankwafo ya sauke min kiss kan kumatu sannan ya É—ago, fuska na É“ata na turo baki gaba murmushi yayi yaÉ—an ja lip É—in na kaÉ—an cikin kasa da murya yace "Idan kika turo shi gaba kyau kike karawa, kamar nayi ta tsosa." hannun sa na bige ina murguÉ—a bakin Æ´ar karamar dariya yayi yace "To ai hakan ma duk kyan yake kara mi." hannu na yarfe nace "Ni ka kyale ni." dariya ya kuma har yana tafa hannu. sannan yace "Ni zan juya daga nan zanje wani guri idan kun shiga kice wa Hajiya zan dawo zuwa anjima." ban amsa shi ba nayi sauri na buÉ—e motar nafita, su Naseem suka biyo ni. Da sallama nashi cikin parlour'n kamar rannan mutane ne tam ciki, yau kam ina yin sallama suka amsa har da yi min sannu da zuwa, wasu Æ´ammata guda biyu suka dube ni da murmushi suna faÉ—in "Sannu da zuwa Aunty HAMDAH matar Yaya Ahmad." da sauri sauran Æ´an cikin parlour'n suka waigo, wasu na faÉ—in "La itace HAMDAH mai *HAM'NAS* Co Petroleum Nigeria Limited." wasu daga cikin su suka basu amsa da faÉ—in "Eh fa itace." nan suka shiga yimin sabuwar gaisuwa. murmushi nayi ina faÉ—in "Sannun ku." wata dake gefen su tana ai kin danna waya taÉ—ago taja dogon tsaki tamike tabar cikin parlour'n, da mamaki nabi bayan ta da kallo, inata son tuna in da na taÉ“a ganin ta, cikin kankanin lokaci na tuna anan gidan na santa ranar da na fara zuwa, itace wacce ta yi mana iso gurin Hajiya. maganar É—aya daga cikin Æ´ammatan nan naji tana faÉ—in "Bari nayi miki magana da Hajiya." nace to. ta shiga jim kaÉ—an ta fito tace "Kishiga tana ciki." naja hannun su Naseem.. nayi sallama bakin kofar daga ciki ta amsa a hankali na shiga ina mai kara yin wani sallamar. tana hakimce kan wani tattausan dadduma ta kishin giÉ—a da wasu filulluka na alfarma. fuska ta faÉ—aÉ—a da murmushi tace "A'a manyan baki ne haka, sannun ku da zuwa ku karaso nan ga gurin zama." ta nuna min gefe da ita. na karaso na zauna tare da gaishe ta ta amsa tana washe baki da shafa kan su Nasmah. tace "Ina shi Ahmad É—in?." nace "Yace nace miki zai dawo anjima yatafi wani guri ne." kai ta jinjina ta mike zaune. hira tari jana dashi, niko sai binta da murmushi nake wani bin kuma na amsa mata, ina mai jin nauyin ta. har aka kira sallar azahar muna zaune tana ta jana da hira, na É—an muskuta nace mata zanyi sallah. tace nashi ga bayin nan cikin É—akin, bayan nayi al'wala na fito na tarar bata É—akin har da su Naseem, nagabar da salla, ina zaune ina tasbihi ta shigo wata na biye da ita da tray mai dauke da kayan abinci, ta dire a gefe na sannan ta fita. Hajiya ta zauna tana faÉ—in "Yaran nan sun sami Æ´an uwan su yara suna can suna ta kan wasa." murmushi nayi nace "Ai su Naseem akwai son wasa." tace "Yaran kenan ai kai babba wace wasa zaka tsaya yi, ai sai dai in akwai wasan nera to kaÉ—ai zaka tsaya kayi shi." "Uhm." kawai nace badun da fahimci karin maganar nata na karshe ba. tray'n abin cin ta tura min gabana tace naci. É—an sakurar abincin nayi dan bana jin yunwa, na tura tray'n gefe ina faÉ—in "Nagode." tace "Nayi zaton zakici da yawa dan gidan nan babu kaÉ—an komai mai yawa ne." "Nakoshi ne." nafaÉ—a a takaice tare da yin murmushi.. Zaman ta ta gyara da kyau kana taÉ—an sunkuyo in da nake a hankali ta soma magana "Ai ita kogi bata ki yayyafi ba komi akwai É—in ka zaka so kari, ko ba haka ba?." kai na gyaÉ—a ina cigaba da murmushi bawai kodun sanin inda batun nata ya dosa ba. baki ta kuma washewa tana mai jinjina kai kana ta daÉ—a gyara zaman ta kana a hankali tace "HAMDAH." takira sunaan, na amsa tare da duban ta jin yanda ta kira sunan nawa a sama, tace "Kuna lafiya dai babu komai ko." kai na gyaÉ—a ina mai kuma amsa sabuwar gaisuwar nata. ta mike ta fita jim kaÉ—an ta dawo, É—auke da plt ta dire a gabana, ta ce "Ki ci wannan wata kila zai fi miki sauran." kallon plt É—in nayi tare da yin murmushi dambun naman kaza ce a ciki sai tashi da kamshi yake, nace "Nagode." É—an shiru tayi taÉ—an waiga gefe da gefe kamar mai duban wani abu sai kuma ta kuma mai da hankali ta kaina cikin yin kasa da murya tace "Akwai maganar da nake so muyi yanzu mai mahimmanci ne zaÉ“i kuma a gare ki, moriya da amfanuwa duka." kai na jinjina ina mai sauraren ta. tace "Shi arziki kogini idan ka yi tsayuwan daka wajen niman sa samun sa bazai taÉ“a baka wuya ba, kina da kuÉ—i kin san daÉ—in su na tabbata ayanzu irin su dubu idan zaki samu ba zaki ki son su ba." shiru nayi ina sauraran ta cikin rashin fahimtar in da batun nata ya dosa. a hankali ta mike ta isa can gaban gado ta É—au Laptop saman bedside ta dawo in da nake ta zauna agefe na akasa in da nake zaune, kana ta kunnan Laptop É—in ta daddannan sannan ta aje a gabana. hotuna da bidiyoyin kaddarori ne suka rika bayyana ciki, manya manyan gine gine gidaje masana'antu daga nan gida Nigeria har kasashen ketare, ido na ware ina kallon tulin tarin dukiyar, da bansan ma'anar nuna min shi da take ba. zuwa can ta saki dariya tare da rufe Laptop É—in tace "Wannan kaÉ—an ne daga cikin dukiyar Alhaji Tijjani Sabil wan da ayan zu yazamo mallakin Ahmad Tijjani Sabil, bayan tulin dukiyar da shi kansa Ahmad É—in ke da shi, HAMDAH." takuma kiran suna na tana mai dubana da kyau sannan tace "A rayuwar nan na yanzu baka da burin daya wuce kazamo abin kwatance aduk in da kake duk in da ka shiga arika nuna ka, kayi fintinkau cikin kawayen ka, misali kamar ke a yanzu da kika zamo abin faÉ—a, na tabbata kina so kida É—a fin haka, idan kuma kinso a yanzu zaki fi hakan cikin sauki zaki daÉ—a mallakar dukiya mai tarin yawa, ki É—aukaku a duniya, cikin sauki idan kina da bukata a yanzu zaki iya zamowa haka." shiru nayi ina sauraran ta da É—inbin mamaki cikin raina, taya za'ayi nasami wannan dukiyar datake ta misalta min shi É—innan? ai ko lokacin da nasami dukiya ban samu ta sauki ba sai da rayuwa ta dana Æ´aÆ´ana takusa salwanta, amma kuma take cewa zan sami ninkin ba ninki kuma cikin sauki, to ni wace É—aukaka kuma É—aukakar da Allah yayi min yanzu ma na gode masa.. katse min tunani tayi da faÉ—in "Kin shiga tunanin ta ya hakan zai kasance ko?." sai ta saki wani dariya tare da cigaba da faÉ—in "Cikin ruwan sanyi ma kuwa, idan kika haÉ—a kai dani zakiji daÉ—i idan kuma kika bijire zaki faÉ—a cikin halaka, ina nufin rayuwar ki zata salwanta." ido na waro da sauri na É—ago na dube ta, wani irin hatsabibin murmushi ta sake kana ta girgiza kai tace "Kwarai kuwa, kin auri Ahmad bawai dun kina son sa ba sai dun son da shi yake miki, nasami labari sosai kan cewa bakya son shi kuma ina da tabbacin cewa har yau ba son na shi kike ba, me zai hana muhaÉ—a karfi da karfe kibi ta wannan hanyar kici moriyar dukiya mai tarin yawa, ki kara kan naki, ki daÉ—a zamowa abin kwatance a duk faÉ—in kasar nan da ketare baki É—aya." Zuwa yanzu maganar nata yafara jefari cikin firgici da tsoro dan na rasa me take nufi dahar zata yi min barazana da salwanta rayuwa ta. É“ari jikina ya soma a raina nake faÉ—in "Innalillahi'wa'inna'ilaihirraju'un,abin da nayi gudu shiyake kuma tunkaro ni." maganar ta najiyo tana faÉ—in "ZaÉ“i yarage naki idan kin so a yau zaki iya aiwatar da komai." ta mike tsaye taje taja drower har ta dawo ta zauna in da ta tashi kaina na sunkuye, yayin da firgici mai tsanani ya shige ni, sai nanata kalmar Innalillahi'wa'inna'ilaihirraji'un nake. "Ungo karÉ“i rike wannan." da sauri na É—ago ina duban abin da take mika min É—in wani kullin magani ne cikin laida, hannu na na É“ari na karÉ“a tare da kura masa ido. tace "Wannan maganin shine hanya mafi sauki da zakibi ki mallaki dukiya mai yawa ki kara kan naki, ki zuba wa Ahmad a cikin abinci ko sha, idan yaci zai kwanta jinya ba kada kiji tsoro dan ko likitoci bazasu taÉ“a gane wani abu yaci ba, kuma baza'a taÉ“a gane ciwon me yake damin sa ba a haka zai tafi daga nan kuma zance ya kare, zamu raba dukiyar biyu ki É—auki rabi na É—au rabi, tun rabar dana sami labarin auren ku na kasance cikin farin ciki dan na tabbatar zaki iya aiwatar wa tun da ba son shi kike ba." wani irin É“ari hannuna da ilahirin jikina suka É—auka cikin tsananin mamaki tashin hankali na É—ago na dube ta murya na rawa nace "Kashe shi za'ayi." wani irin kafurin dariya tayi tace "Kwarai kuwa nasan aiwatar da hakan bazai baki wuya ba tun da bason shi kike ba, ko da ace kina son shin ma so É—in banza kuÉ—i ai yafi miki shi, yana mutuwa kuma zaki sami wanda yafi shi." gaba É—aya Æ™waÆ™walwa ta ya tsaya cak ya daina ai ki firgici da tashin hankali su suka dabaibaye ni, ta ko ina É“ari yake a jiki na. kisa nice zan kashe mutum da hannuna wai uwa ce ke son gusar da É—an ta anya ba mafarki nake ba?, da sauri na mussuke idanuna ina mai ware su a kanta maganar ta na natsinkayo a sama "Kada ki É“ata min shiri yin hakan babban kuskure ne, na tabbatar miki rayuwar ki dana Æ´aÆ´an ki zasu salwanta, kiyi tunani ki dubi tulin tarin dukiyar nan ace sudaÉ—a zamowa mallakin ki ki zamo abin nuni da faÉ—a a duniya, ba pillow zaki danne kansa da shi ba ba kuma wuka zaki daÉ“a masa aciki ba, wannan kaÉ—ai zaki zuba masa cikin abinci daga nan shike nan arziki ya dawo naki." hannuna mai maganin ta rike ta kalle ni tana dunkule min maganin cikin hannuna, cike da karfafa guiwa ta cigaba da faÉ—in "Kada kiji tsoron komai ko ki tsaya tunani ki rika tuna tulin tarin dukiyar nan ki ai watar kada kiji komai babu wan da zai zarge ki dan babu ta in da za'ayi a gane, kuÉ—i yafi komai a rayuwa." maganin ta karÉ“a a hannuna taÉ—au jakata ta jefa shi ciki tarufe tana faÉ—in "Ki kula kada a sami matsala faruwan hakan babban matsala ce ga rayuwar ki." kai na girgiza da sauri, murmushi tayi zata kuma magana akayi sallama daga bakin kofa, zaman ta ta gyara da sauri taÉ—an matsa gefe, Ahmad ne rike da su Naseem a hannun sa suka karaso suka zauna, fuska ta faÉ—aÉ—a da murmushi tadubi Ahmad tana faÉ—in "Sannu Ahmadu numfashin Sabil an dawo." yace "Eh Hajiya bar ka da gida." tace "Yauwa Ahmad Allah yayi albarka ya tsare gaban ka da bayan ka." "Amn amin." ya amsa yana mai murmushi. ya mike ya dube ni sannan yace "Muje ko yau kinyi wa Hajiya wuni." da sauri tace "A'a kam sai dai rabin wuni dai, tamayi kokari a hakan dan tafi wancan Rasheedat É—in mai isa da kafafa." murmushi kawai yayi, yayi waje tare da É—aga kiran da ya shigo wayar sa yanzu. jiki a sanyaye na mike, itama ta mike tare da É—aukar jakata ta mika min sannan ta dube ni da kyau tace "Ki kula ki ai watar da komai ya tafi dai-dai kada a sami wata matsala, ni zan kula da komai daga baya, ki kawar da abin da bakya so ki kuma sami karin dukiya mai yawa, ki É—aukaka a duniya, kada kiji komai zan tsaya miki." ta dafa kafaÉ—a ta tana mai kuma jaddada min. yau ma har kofar parlour ta yi min rakiya tana, ina dai-dai zama ta cikin motar na sauke numfashi da karfi har sai da ya juyo ya kalle ni. a hankali na maida baya na na jingina da jikin kujerar motar, gaba É—aya jiki na ya gama sanyi. gefen da nake ya waigo ya dube ni kana ya mai da duban sa kan titi yace "Madam ya dai?." idanuna na lumshe batare da na amsa shi ba.. har muka isa gida idanuna a lumshe yake yana gyara parking najiyo Muryar sa daf da ni yana faÉ—in "Ko na É—auke ki nashi da ke ne?, naga kamar kin gaji." a hankali na buÉ—e idanuna na jiki a sanyaye kai hannu na buÉ—e marfin motar nafita.. Ina shiga bedroom na wuce bathroom da sauri na shiga tube kayan jiki na dan gaba É—aya wani irin a zabebben zafi nake ji, tun daga ta ciki na har waje. na daÉ—e cikin ruwan sanyi kafin na fito, duguwar riga mara nauyi na zura a jiki na batare da pant ko bra ba, na zauna bakin gado yayin da maganar Hajiya ke tayi min yawo cikin kwakwalwa. jakata na É—ago na buÉ—e na ciro maganin ina juyashi a hannuna yayin da bugun zuciya ta ta karo. "Innalillihi'wa'inna'ilaihirraju'un, me yamata haka take son kashe shi? sabo da kuÉ—i?, kuÉ—in da zaka mutu ka barshi meye haka da tsanani É—anka ka kashe shi da kanka sabo da son abin duniyar da zaka mutu ka barshi, ba zan iya kashe mutum ba ba zan taÉ“a zamo sanadin wata raiba, da ma nasan babu komai cikin rayuwar aure face kunci da bakin ciki, gani na kuma faÉ—a wa cikin wani ahalin da suke son ganin bayan junan su, meye nawa da zasu so jefani ciki dama ni na sani a haka rayuwa ta zata kare." wani irin kuka ne mai matukar tsuma rai ya kwace min, sai na toshe baki na nashiga rusar kukan. a hankali aka turo kofa, da sauri na dunkule hannuna mai rike da maganin nayi baya da shi da sauri na É“oye shi a bayana, É—aya hannuna dana toshe baki na nashare hawaye na da sauri na haÉ—iye kukan. a sannu yakaraso cikin É—akin, ban yadda mun haÉ—a ido da shiba kaina a kasa, na É“ata fuska. a gefe na ya zauna muna fuskantar juna. ya É—an tsunkuyo tare da leko fuskata yace "Kyakkyawa ta bacci kike azaune ne?." baki na turo gaba, yayi murmushi tare da faÉ—in "Ashe dai idanun ki biyu." hawayen da nake ta makewa ne suka gangaro, ido ya tsura min na É—an wani lokaci batare da yayi magana ba, yayin da hawayen suka ci gaba da gudu babu ko kakkautawa. da karfi yaja numfashi tare da furzar da iska mai zafi daga bakin sa, hankali tashe yashiga girgiza ni da faÉ—in "HAMDAH me ya faru me ya same ki!?." cikin muryar kuka nashiga faÉ—in "Nace bazanyi aure ba arabu da ni a ka matsa min dole sai da nayi shi, bayan na riga da na sani babu komai cikin sa sai zallar kunci da tashin hankali, me yasa kuke da son kan kune? me yasa kuke son ganin bayan rayuwa ta?,me nayi muku? ni banyi muku komai ba hatta Æ´aÆ´an da suke ciki basu san komai ba basu É—au alhakin kowa ba sai da aka zalunci su, har sun fito duniyar ma baza a barsu su huta ba?, me muka yi muku me muka tsare muku!?." kuka ne sosai ya kwace min nashiga rera shi. ido ya tsura min yayin da kamannin sa ya sauya gaba É—aya fuskarsa ya rikiÉ—e daga nashi na kullum mai fidda annuri da fara'a, ya koma izu fuskar fusatattaun maza. ya janyo ni jikin sa ya rungume ni da kafi kamar zai É“alla ni, da karfi-karfi yake sauke numfashi yayin da kirjinsa yake bugawa da karfi har ina iya jiyo sautin sa, kasan cewar kai na yana cikin kirjin nasa. zuwa Æ´an wasu mintuna, sai yashiga sassauta rukon da yayi min É—in, yayin numfashin sa ya dai-dai ta, a hankali yashi ga shafa kaina yana É—an bubbuga baya na. a hankali yasoma magana sai dai sautin maganar nasa yana fita da amon sauti mai É—an kara, "Idan har ina numfashi nayi miki alkawarin babu mai kuma saki kuka,bare har su taÉ“a bayin Allahn da basu taÉ“a aikata zunubi ba, zan zame muku garkuwa da yardar Allah." shiru ya É—an yi sai kuma ya saki murmushi mai sauti, ya leko fuskata dake cikin kirjin sa sannan yace "Ke da aka baki kwangila madadin ki ai watar sai ki zauna yin kuka." wani irin rasss gaban kirji na ya yanke, me yake nufi kada ace dai ya gane abin da Hajiya ta bani na aiwatar a kansa.. maganar sa ce ta katse min tunani "Tana mance wa da cewa Allah shike da ikon rayawa da kuma kashe wa, waÉ—an da tayi sanadiyyar kashe su ma Allah ne ya nufa kuma lokacin su ne yayi, bata da ikon kashewa a hannun ta Allah shi kaÉ—ai yake da iko." zuwa yanzu kam numfashi na ne ya so É—auke wa, da sauri na ciro kai na a kirjin sa tare da zuba masa ido. hannun sa ya mika ta baya na ya ruko hannuna dake rike da maganin dana É“oye shi ta baya na, ya buÉ—e tafin hannuna yaciro magani, ya dago shi yana jujjuyawa a hannunsa sai kuma ya saki murmushi mai sauti idanun sa cikin nawa yace "Yaushe ne zaki saka min shi cikin abincin?, amma dai yau da hannun ki zaki girka min mai daÉ—i ko?." ya karasa maganar da É—aga min gira. Idanuna na rumtse da kafi nakuma buÉ—e wa a kansa kai ya langwaÉ“ar gefe yace "Kin gani ko kiyayyar da kike yi min har ta bata kofar son cimma burin wasu, Hajiya Karima ta yi sanadiyyar mutuwar Baba na, sabo da son abin duniya,tasa aka kwance masa tayar mota ta sanadiyyar haka yayi hatsari a take yarasa rayuwar, bayan rasuwar sa da kwana uku, mahaifiya ta tajisu suna maganar da waÉ—an da ta sasu suka ai watar da haka, ta sanadiyyar haka mahaifiyata ta kamu da ciwon zuciya sabo da bata da hujjar da zata kawo damin a kama Hajiya Karima da waÉ—an da tasa sukayi mata aiki, tayi ta fama da ciwon bada jimawa ba itama ta rasu da bakin cikin abin da Hajiya Karima ta ai kata, tun daga lokacin ta fara sarkafar rayuwa ta dan a cewar ta sai ta gusar da ni kafin ta samu mallakar dukiyar mahaifina duka har ma da nawa, tun bayan rasuwar mahaiyata ta mallake gidan mu ita da Æ´an uwan ta, duk waÉ—an nan mutanen da kika gani cikin gidan mu Æ´an uwan ta ne, tabi ta hanyoyi da dama bata sami cimma burin ta a kaina ba, sai ta turo É—iyar É—an uwan ta wacce dama tun mahaifana na da rai taso haÉ—a ni da ita, idan baki mance ba yarin yar da ta gaishe ni ban amsa gaisuwar ta ba, ranar da muka fara zuwa gidan da ke, sai naki amin ta, da gaske Sakeenat tana sona, bata kuma yarda da muradin Hajiya na bayan munyi aure ta gusar da ni ba, da kanta ta faÉ—a min takuma bani tabbacin bazata iya kashe ni ba dan tana sona, na kore ta na mata kaca-kaca nace kuma kada ta sake kawo min kwatankwacin irin wannan maganar tayi wa Hajiya sharri ne, nasan komai nakuma ki nuna mata cewa na sani tun ranar da mahaifina ya rasu nasan dukkanin shirin ta, har kuma rana mai kamar ta yau a tafin hannuna take komai." ÆŠan sakaita maganar yayi tare da jan numfashi sannan ya cigaba da faÉ—in "Sai gashi yau tabiyo ta hannun ki da tabbacin ke zaki iya sabo da labarin data samu na bakya so na." ido na zuba masa ciki matukar tausaya wa hakika labarin ya jijjiga ni yakuma bani matukar tausayi, duk da sanin shirin nata amma yake tare da ita yake yi mata kallon uwa da har nayi tunanin ita mahaiyar sa ce, me yasa ya barta take rayuwa bai É—auki mataki a kanta ba, bawai kuma dan bazai iya ba, duk tulin tarin hujjujin da ya ke da su É—in na.......! Mommyn Twins ce 8/19/22, 10:57 - Ummi Tandama😇: 23 Nace "Wlh Allah ban yarda ba, shine zaka yi amfani wajen gusar min da tunani na." dariya sosai yayi yace "To hakuri zakiyi kuma ai kema kin rama, ba nima kin gusar min da tunanin nawa ba jiya, kuma ai ke kika sa na aikata hakan son ki na shirin kashe ni da sauran kwana na, bukatar ki na shirin illata ni kin san da ya na kwana shekaran jiya, shi yasa kawai na ai watar da haka ba gashi na samar wa kaina mafita ba, zo kiji yan da akayi." ya ciro ni daga jikin sa ya zau kan kujerar gaban mirror kana ya zaunar da ni kan cinyar sa, ya zuro hannunsa ya zagaye ni ta gaba tare da ruko hannaye na da kowa ni hannunsa yana É—an murza su kana ya soma magana "Ban san sha'awa yana sanya ciwo ba sai da na zo gare ki shekaran jiya, marana kamar zai fashe, na kwana cikin mawuyacin hali, da safe na shirya natafi pharmacy domin sama wa kaina magani, to mai pharmacy mutumi na ne bayan nayi masa bayanin abin da yake dami na sai ya bani magani, har na fita na shiga mota sai ya biyo ni har cikin motar, ya bani maganin nan yace na zubawa Madam a cikin abin sha tasha magani na yana gurin ta, dan maganin da ya bani zai iya lafawa ne yanzu anjima ko gobe zai iya tashi min, amma idan nayi amfani da wannan zan sami ingantaccen magani a gurin ta zan warke, na karÉ“a nayi masa godiya, ina dawowa gida kuwa shine naje na É—au yoghurt a fridge na zuba a ciki, na ajiye akan idan na dawo daga masallaci nazo na baki kisha, duk da nasan da kyar ki amince ki sha, sai gashi cikin sauki Allah ya taimake ni yaji tausayin bawansa da so ke kokarin ajalin sa, da kanki kikaje kika É—auka kika sha, kuma banyi ba sai da amincewar ki. niko nayi ta zunduma cikin rijiyar ina kwasar ruwa, kai kinji yan da kika rika bani shi kuwa nace wayyo Allah ashe haka yarinyar nan takware wajen iya mika abin, kai kinfa birkita min lissafi ba kaÉ—an ba. muÉ—an je ki É—an kara min ne ko É—an kaÉ—an ne." gaba É—aya kunya yagama lulluÉ“e ni, kai wannan mutumin bashi da kunya shi gaba É—aya baya iya É“oye maitar sa, da sauri na yunkura a jikin sa zan mike cike da jin kunya. yayi saurin maidani yana dariya. yakawo bakin sa saitin kunne na a hankali yace "Baza ki bani na safiyar ba." kafaÉ—a na make yace "A taimaka dai." baki na turo gaba nace "Allah idan ka sake samin maganin nan bazan yarda ba." yace "Bazan kara ba idan na kara kema ki rama, muje muyi breakfast jiran ki nake dama ki tashi muyi." Ya mikar dani tsaye ya ruko hannuna muka fito parlour. kin cin abinci nayi na zuba nazuba masa ido, yace "Kici mana kyakkyawa ta buÉ—e baki na saka miki." kafaÉ—a na make nace "Ni bazan ci." murmushi yayi yace "Ai nayi alkari bazan sake sa miki ba Allah babu komai a ciki muci kinji." da kyar yayi ta lallaÉ“a ni har na yarda naci. amma hankali na yaki kwanciya har saida naga na kai wani lokaci ban ji wani sauyi tattare da ni ba. A ranar Ahmad yaki bari na ko yamatsa in da nake yana nan like da ni, zolaya kuwa na shasa a gunsa tun idan yayi ina jin haushi har yadawo bani dariya, da kyar na samu na zame jikina nashiga bathroom, nacika ruwan É—umi cikin bathtub nashige ciki, dan har yanzu HQ É—ina yana yi min zafi, da sauri na É—ago jin ya turo kofar, fuska na É“ata ina kare jikina da hannaye na. ya karaso ciki ya tsaya a kaina yana kare min kallo, nace "Meye haka kafita mana." kayan jikin sa yashi tuÉ“e wa yana faÉ—in "Idan nagama wankan kenan ko." da sauri na mike na janyo towel ganin ya zare wandon jikin sa, ina kokarin É—aura towel É—in ya fisge ya mai da shi ma'ajiyar sa, kana ya shige cikin bathtub É—in, ya ruko kafaÉ—a ta ya mai da ni zaune shima ya zauna. ya mikar da kafafun sa, ya ware nawa da su ya danne nawa, kana ya janyo ni sosai yayin da joystick É—in sa ke gogar HQ É—ina. kallon cikin ruwan yayi in da joystick É—in sa keta harbawa yana gogar HQ É—ina, kana ya dube ni a marairaice yace "Kin ga in da yake son shiga." idanuna na rutse da karfi, cikin matsananciyar jin kunya, nayi yu kurin mikewa amma na kasa. batare dana buÉ—e idona ba nace "Ni karabu da ni bana so." murmushi mai sauti yayi a hankali naji saukar hannunsa kan ababen kirji na, sai ya rika É—iban ruwan yana zubawa a kansu yana kuma matse su, da sauri na buÉ—e ido jin yana kokarin tura joystick É—in sa cikin HQ É—ina. da karfi na daddage nashiga ture kirjin sa ina faÉ—in "A'a ni dai ka kyale ni." idanunsa da suka fara sauyawa ya zuba min murya a cushe yace "Ko kaÉ—an ki taimakawa bawan Allah da son ki ke shirin zautar da shi." hararar sa nayi ta gefen ido, murmushi yayi yana manna min kiss a goshi. da kyar na daddage na samu na janje jikina nayi baya, dan naga da gaske yake ta son zurma abar tasa. kan ya ankara na fita cikin bathtub É—in na jonyo towel na É—aura nafita a bayin da sauri.... ( *Bauchi state* ) G.R.A Wani irin razani da birkita SALEEN yayi a lokaci guda ya mike zaune har jikin sa na cirawa, tare da dafe kirjin sa da karfi. Na'ima da shigowar ta É—akin kenan da sauri ta karaso in da yake, ta dafa kafarsa tana faÉ—in "Lafiya My SALEEM wai me ke damun ka ne, sakanin jiya da yau kake ta firgita cikin bacci?." idanunsa ya rumtse da karfi, ya cusa hannayensa cikin sumar kansa ya yamutsa tare da furzar da huci mai zafi, da sauri ya duro a gadon ya shiga bathroom yasakarwa kansa ruwa mai sanyi sosai, yayin da yake sauke wasu irin tawayen numfarfashi mai haÉ—e da huci kamar wan da yayi tsere. ido Na'ima ta zubawa kofar bayin, ita fa abin nan yafara damin ta tun jiya da daddare suna kwance yayi wani irin zabura kamar mai tashin aljannu, gaba É—aya yafita hayyacin sa, still gashi yanzu ya sake maimaita irin haka. kai ta girgiza tana faÉ—in "Nasan ko zan yi yaya da bakin sa bazai faÉ—a min ba dole naje gurin boka naji me yake faruwa." Tana nan tsaye har ya fito ya wuce ta yaje ya sauya kaya, ta tako in da yake ta rungume sa ta baya a hankali cikin muryar kirsa da makirci tace "Haba My SALEEM idan baka faÉ—a min damuwar ka ba mawa zaka faÉ—a mawa, wlh karkaga yan da hankali na ya tashi, anya ba magauta ke bibiyar ka ba?." zame jikin sa yayi yaÉ—an juyo ya kalle ta sai kuma ya juya yanufi in da makullin motar sa yake ya É—auka yayi waje... A hankali yake tuki kamar mai tausayin titi, gaba É—aya yanayin sa ya sauya jikin sa yayi sanyi kamar wanda ruwan sama yabige shi. a haka ya isa family H É—in du, yana dai-dai ta parking ya fito a hankali ya nufi side É—in Mamie. a parlour ya yasame ta tana zaune tana kallon labarai, ya isa ya zauna sannan yashiga gaishe ta. sama-sama ta amsa masa dan har yau bata sake masa, tun da ta amsa gaisuwar kuwa ta mai da idanunta kan TV, ya karaci zaman sa ya mime yayi mata sallama can kasa ta amsa shi ya fita. Side É—in Ummi ya zarce yayi sallama ya shiga, babu kowa cikin parlour'n ya karasa ya zauna kan É—aya daga cikin kujerun parlour'n. Ummi dake cikin bedroom tana zaune kan sallaya tana jan jarbi tajiyo sallam, ta mike ta fito can ta hango shi zaune yayi jigum. ta karaso in da yake da murmushi É—auke a kan fuskar ta "Ah SALEEM kai ne? sannu da zuwa ya gidan da mutanen gidan, ina ango shine ba'a zo min da shi ba?." gajeren murmushi yayi, yana gaishe ta, ta amsa cikin sakin fuska, kana ta mike taje ta je kitchen ta taho masa da abinci da ruwa kamar yanda ta saba, a koda yaushe idan yazo gaishe. zaman sa ya gyara a kasan carpet yashiga cin abincin da ta zuba masa cikin plt, yaci da É—an dama kana na kara da ruwa. Ummi tayi ta jansa da hira hm da um shine kawai amsar sa. ya É—an jima zaune kana ya mike yayi mata sallama, Ummi tazuba wa bayan sa ido dan yana yin sa yafi kama da wan da yake cikin damu sosai. daga gidan offece ya wuce haka ya wuni bai taÉ“uka komai ba... *Abuja* Bayan sallar la'asar ina tsaye cikin bedroom Ahmad ya shiyo dawowar sa daga masallaci kenan, hannunsa rike da makullim mota, ya taho in da nake, rungume ni yayi tare da sumbatar goshina yace "Kyakkyawa ta, kin hana ni kari ki gani har dare ya fara yi, haka zan tafi baza ki É—an kara min?." kafaÉ—a na make, murmushi yayi yana daÉ—a janyo ni jikin sa yace "To bari naje na É—auko su Nasmah, kada a barki ke kaÉ—ai ko zamu tafi can É—in ne jibi sai mu dawo?." harara na dalla masa ina zame jiki. da sauri ya taro ni yana dariya yace "Afwan kada ayi min hukuncin daban iya É—auka ba." bakin sa ya manna kan nawa yayi kissing É—in sa sosai kana ya sake ni yana bina da murmushi har ya fita. numfashi na sauke tare da zama bakin gado... daf magriba motar sa tashigo gidan, ina zaune a parlour'n kasa ya turo kofa da sallama, su Naseem dake bayan sa suka shigo da gudu, Rasheedat na biye da su, a jikina suka zube suna faÉ—in "Oyoyo Mommy, Mommy kin dawo ne?." murmushi nayi tare da shafa kan su nace "Eh nada wo." Naseem yace "To Mommy ina tsara bar mu?." Nasmah tace "Kin kawo mana tsaraba?." kai na gyaÉ—a nace "Nakawo muku yana É—aki." ihun murna sukayi suna daÉ—a É—alewa jikina. Rasheedat dake ta binmu da murmushi tace "Iye-iye amma dai zaku sanmin tsarabar taku ko?." sauka sukayi daga jikina suka koma jikin ta suna faÉ—in "Eh Mamy damu baki da yawa da yawa." ido ta waro tace "Kai amma naji daÉ—i na duka ni kaÉ—ai." murmushi nayi ganin yan da take ta yi da yaran kamar zata goya su dan so, tabbas duk wan da yaso naka yagama maka so a duniya. ta juyo in da nake tana faÉ—in "Wato shine zaki kwace min su yau ko?." murmushi nayi nace "Ina yini Aunty Rasheedat." fuska É—auke da annuri tace "Lafiya lau kin dawo lafiya ya gajiyar hanya?." nace "Alhmdllh." ina dago wa muka haÉ—a ido dani, baki na murguÉ—a masa, shiko wani murmushi ya sake tare da jingina bayan sa da jikin kujera yana bina da kallon kasan ido. kiran sallar da aka fara yi ne yasashi mike wa yafita zuwa masallaci, na dube ta ganin yan da ta shagalta da biyewa yaran. ta mike tana faÉ—in "Mujen ku muyi salla ko." nace mata mu haura sama, tace a'a zata yi a kasa kawai. nan bayin kasa tayi al'wala da yaran a nan parlour sukayi salla. ni ma anan É—in nayi al'walar nayi sallan. koda muka idar hira sosai Rasheedat tayi ta min har aka kira isha, sai da aka idar kafin Ahmad ya shigo. ya zauna aka cigaba da hiran da shi, duk da ni bawani amsa su nake ba, iya kace idan sukayi abin dariya na É—an murmusa, haka suka yi ta jana da hiran. a É—an zaman mu da su yanzu na fahimci suna da kyakkyawar fahimta sakanin su. sai wajen karfe goma sukayi min sallama lokacin tuni har su Naseem sunyi bacci. tana gaba ya na biye da ita, tana fita ya dawo da baya da sauri ya rungumo ni yace "Zanyi missing É—in ki." bakin mu ya haÉ—e ya tsotsi bakina da kyau kana ya É—ago yana bina da wani irin kallo, a hankali ya sake ni ya juya ya fita. bayan sa nabi da kallo ina mai sauke numfashi, a hankali na taka bakin kofar na rufe kana na juyo. na kwashi su Nasmah na kai su É—akin su, na wuce bathroom É—in É—akin nayi wanka na fito, natafi bedroom É—ina na saka kaya, sannan na dawo É—akin nasu na haye gado nabi ko wannansu da addua, kana na kwanta tsakiyar su ina mai shafa addu'ar da nayi a jikina. a hankali bacci ya dau ke ni can cikin bacci naji wayata na ruru, idanuna a rufe na laluÉ“o wayar tare da É—aga kiran na kai wayar kunne batare da na buÉ—e idanuna ba, muryar sa na jiyo yana faÉ—in "Kyakkyawa ta kinyi bacci ne?." "Um." nace cikin magagin bacci yace "To ki tabbata mun haÉ—u cikin baccin nan kiji, kyakkyawa ta kina jina?." juyi nayi a hankali nadaÉ—a manna wayar a kunne na nace "Eh." yace "Kiyi mafarki na kinji? kiyi mafarkin muna tare kina shayar da ni daÉ—i." idananuna na bude a hankali, jin yan da amon sautin sa mai sanyi ya doki kunne na, a hankali na mai da idanun na lumshe ina jin yana faÉ—in "I love You I love you too, please kiyi tunani na koda na seconds ne kinji? kiyi magana kyakkyawa ta zakiyi?." sinyar kaina nayi da faÉ—in "Um." wani nannauyar ajiyar zuciya ya sauke yace "Ina son ki kiyi baccin ki mai daÉ—i." zare wayar nayi na aje a hankali na gyara kwanciya ta, bawai ko dun na koma baccin ba maganganun sa ne sukayi tayi min yawo cikin Æ™waÆ™walwa da zuciya ta, yayin da amon sautin sa mai sanyi ke yawo cikin kunnuwa ta. a hankali na sauke numfashi..........! Bani da Cj idan na matsa sainayi page mai tsawo to fa wayar zata iya É—auke wa bakuma zaku samu koda kaÉ—in É—in ne ba kunsan matsalar nepa da ake fama da shi yanzu so sai a hankali 8/19/22, 10:57 - Ummi Tandama😇: 22 Ya fizge towel É—in gaba É—aya yayi cilli da shi gefe, ido na rumtss da karfi tare da dukunkunewa guri guda na saki kuka ina faÉ—in "Na rantse kayi gaggawar mai damin towel É—in nan jikina, wlh idan ba haka ba sai na yi maka abin da baka sammani." ido ya kafe ni da shi babu ko kiftawa yayin da ilahirin jikin sa ya É—auki É“ari, wani irin muguwar sha'awa bukata so kauna begen kasantuwa su suka dirar masa suka cushe masa cikin kwanya. numfashi ya ja da kyar hannunsa na rawa yakai jiki na yashiga shafa ni, daÉ—a dukun kunewa nayi cikin muryar kuka nace "Ka daina taÉ“a ni." a hankali yaÉ—an rankwafo zuwa fuskata murya cike da É—in bin fitina da wutar jarabar dake azalzalar sa yace "Kyakkyawa ta kiyi hakuri, bazan kusan ceki ba harsai da amincewar ki, idan kin amin ta da ni kin shirya karÉ“ar bakwanci na,na gabatar da kaina a gare ki, amma ki sani nakai matakin da zan iya samin mummunar illa." numfashi yakuma ja da kyar yaci gaba da faÉ—in "Ina da hakki a kanki kada ki mance girman sa, bakuma zan matsa miki dole a kan sa ba son da nake miki bazai barni nayi miki dole a kan abu ba, ina son ki kuma da sonki zan mutu, har idan baki amince min na kusance ki ba , zan cigaba da jiran ki har ranar da zaki amince min da da kanki ko da ace ranar itace karshen numfashi na a duniya." a hankali ya mike a kaina ya mika hannu da kyar ya janyo towel É—in yarufe min jiki na da shi, wani kuka na sake mai cike da kunar abin da ya min. baya na yaÉ—an shiga bubbuga wa da kyar ya iya furta kalmar "Kiyi hakuri." shima É—in da kyar. ya zamo bakin gadon ya mike da sauri yaÉ—an durkusa ya rike marar sa da karfi, yakai tsawon 10mn a durkushe a gun kana ya mike da kyar yana jan kafa ya fita a É—akin. Kuka nayi ta rerawa da bakin cikin tuÉ“e ni da yayi, a hankali na mike ina jan hanci da faÉ—in "Wani iskan ci yakama ya tuÉ“e ni in dai shi bashi da kunya an faÉ—a masa kowa mara kunya ne." na sauka naje na saka kaya na dawo na kwanta.. A É“angaren Ahmad kuwa a kan gado ya zube yayi ta murkusoso, yayin da yake jin marar sa kamar zata fashe dan ciwo, yayi ta mamaki da tambayar kan sa ashe haka yake ne wai abin ya nashi mamaki dan shi bai taÉ“a sintar kansa cikin irin wannan halin ba, lallai ya daÉ—a yarda HAMDAH ta daban ce. a ranar kuwa bai iya rumtsawa ba haka ya kwana da mugun ciwon mara, washegari bai iya tafiya masallaci ba a gida yayi salla, har wajen karfe 11 yana kwance da kyar ya lallaÉ“a yatashi ya shiga bathroom yayi wanka a daddafe ya fito, ya saka kaya ya É—au makullin motar sa ya fita. wani pharmacy ya je dan bashi da zabin da ya wuce ya samawa kan sa tablet dan yasan koda yaje ga Rasheedat ba lallai bane ta amince masa zatace hakkin HAMDAH ne ya koma gare ta.... Tun da yafita bai dawo gidan ba har yamma, gaba É—aya kewan yara na ya dame ni, ya wani É—auke su ya tafi da su basai ya dawo dasu ba tun da na dawo, kuma ai a gida nake barin su in zanyi yafita ta, waya na É—aga da niyyar in kira shi nace ya dawo min da su, sai kuma na aje wayar na mike ina jan tsaki... da yamma ina zaune a parlour'n kasa yashigo, fuska na É“ata ganin yana ta bina da murmushi har ya iso in da nake ya zauna gefe na, da sauri na matsa can gefe, murmushi mai sauti ya sake ya mika hannu ya ruko hannuna yace "Kyakkyawa ta barka da gida." baki na turo gaba tare da kawar da kaina gefe, mikewa yayi yana cigaba da murmushi ya zo ta gabana ya É—an rankwafo a hankali yace "Zo muje ki tayani wanka mana." da sauri na É“oye hannuna ta baya da yake kokarin ruko shi, saukar kiss naji a goshi na, da sauri na É—ago idanun mu ya haÉ—e guri guda, a hankali ya furta "Kyakkyawa ta yaushe ne zaki fara so na da jin abin da nake ji a kanki?." da sauri na janye idanuna daga nashi ina taÉ“e baki. annurin fuskarsa ya yelwata mai matukar karawa fuskarsa haske da kyau yace "Zaki soni a duk san da muka jone muka zamo abu guda, ranar da zaki karÉ“i bakwanci na." wani kallon shekeke na bisa da shi, shiko murmushi ya kuma kana ya juya yana faÉ—in "To bari na lallaÉ“a naje nayi wankan tun da bazaki tayani ba." har ya É—aura kafar sa É—aya kan step nace "Su Naseem fa suna ina ne?." waigo wa yayi ya dube ni yace "Dama kina son su ne sai yau zaki tambayi in da suke." a hatsale nace "Dama akwai uwan da bata son Æ´aÆ´an ta ne?." "NaÉ—au ka kina daga cikin su ai, zasu dawo amma ba yau ba." yayi maganar yana cigaba da tafiya. kwafa nayi ina bin bayan sa da harara.. ina nan zaune har aka kira sallar magriba, ya sauko cikin shigar tafiya masallaci, tun kan ya karaso na mike da sauri dan nasan sai ya zo in da nake, nashige kitchen, sai da naji fitar sa kafin na fito, na haura sama, ina idar da salla na fito, a hankali na nufi saman dinning in da fridge yake na nufa dan kishin ruwa nake ji, na buÉ—e na ciro garar ruwa mai sanyi haÉ—e da cup dasuke a jere gefen fridge É—in, na tsiyaye ruwan na sha. kana na mai da ragowar ruwan, har zan rufe fridge É—in sai idanuna ya sauka kan wani yoghurt dake baki-bakin fridge É—in ya É—au tsayi har bayan gorar yana zufa, na É—au gorar haÉ—e da cup na rufe fridge É—in na koma É—aki. a bakin gado mazauna na bude gorar na tsiyaya yoghurt É—in cikin cup, a hankali nakai cup É—in baki na É—an kurÉ“a, a hankali na lumshe idanuna jin daÉ—in yoghurt É—in da sanyin sa ya baibaye min baki. narika kurÉ“ar sa ina sha cike da jin daÉ—in sa, har sai da na shanye wanda nazuba cukin cup É—in nakuma karawa, sai da naji cikina ya cika tam kafin namike nashiga bayi na kuskure bakina na fito na haye kan sallaya jin an tada sallar isha, wata doguwar hamma na sake cikin sallata a raka'ar karshe, yayin da naji ilahirin jiki na yana yimin wani iri, a haka na idar da sallar, yayin da nake tajin yanayin na daÉ—a karuwa, idanuna na mutstsuke da duka hannaye na biyu na mike tsaye tare da yin mika dana ji ya taho min babu zato ko sammani. a hankali na ninke sallayar na kai ma'ajiyar sa haÉ—e da hijibin. na dawo bakin gado na zauna, na É—au wayata ina É—an daddana shi. mika na kuma yi, cikin jin yanayin dake daÉ—a shiga ta, nakasa tantance yanayin. aje wayar nayi na gyara na kwanta tare da lumshe idanuna, shiru nayi a hankali nake daÉ—a jin abin da nake jin na karuwa, a hankali na mirgina tare da yin mika na kankame jikina tare da buÉ—e idanuna da suka gama sauyawa kamar me maye, hannuna na cusa sakankanin cinyoyi na na matse da karfi. jin karar buÉ—e kofa yasa ni buÉ—e idanuna a hankali na zubawa kofar, daga bakin kofar ya tsaya yazuba min ido, kana ya mai da duban sa kan gorar yoghurt É—in da ke aje tsakiyar É—akin. a sannu ya tako ya iso bakin gadon ya rankwafo kaina yace "Kyakkyawa ta." shiru nayi na mai da idanuna na lumshe. sosai ya kura min ido ina jin yan da idanunsa yake yawo a jikina, hannu ya sauke gefen fuskata ya shafo a hankali yace "Ya dai kyakkyawa ta wani abun ne?." a hankali na buÉ—e idanuna dasuka gama sauya wa nazuba masa sai kuma na mai da idon na rufe. takun tafiyar sa naji na buÉ—e ido na zubawa bayan sa har ya fita. juyi nayi nakuna sakin dogon mika. ido na waro cikin matukar mamakin gano yanayin da nake ciki, da sauri na mike ina tangaÉ—i kamar Æ´ar kwaya na shige bathroom, kayan jikina natuÉ“e da sauri na cika ruwan zafi nashige ciki, ina mammatse ido, shiru nayi ina jin É—umin ruwan na ratsa ni. madadin saukin yanayin sai ji nayi kamar daÉ—a karuwa yake, nasha mamakin kaina da abun da nake jin. da sauri na fita na zo gaban wardrobe naciro rigar bacci na zura ban ko tsaya tantance wata iri ce ba bare na kaiga sa pant, dan nakai kololuwa wajen jin filling. sai da na saka naga bata karasa kai guiwa ta ba, mai tsiririn hannu ce da gidan bra.. baya nayi na zube kan gado tare da cusa hannaye na sakankanin cinyoyi na, nashiga juya kai cikin mawuyacin hali. wace irin sabuwar al'amari ce ke faruwa da ni yau?. hawaye yashiga zubo min nazube kan gado nayi ta juyi ina matse cinyo yi na, wai ko dun zanji saukin abin da nake ji, amma ina babu sauki cikin lamarin, a hankali na mike zauna jin wuya na ya bushe kantakarau sai haÉ—e miyau nake da kyar, ragowar yoghurt É—in da nasha É—azu nasha na rage na É—auka na kafa kaina sai da nashanye duka na ajiye gorar, na koma na kwanta. nan ma juyin na cigaba da yi gaba É—aya nagama jikewa, tamkar daÉ—a ruramin wutar abin da nake jin ake. Zumbur na mike tsaye ina jan kafa na fita, can na hango shi zaune cikin parlour yana kallo, jin karar buÉ—e kofa yasa shi juyowa ya zuba min ido dai-dai lokacin da nasaki wata doguwar mika. idanuna na matse da karfi kana na buÉ—e, a sannu nashiga É—aga kafafu na nazo na wuce ta gaban sa, dinning na haura nabuÉ—e fridge naciro garar ruwa na kafa kaina nasha sosai. ruwan na shiga cikina tamkar daÉ—a angizo min da wata muguwar filling yayi, sake gorar nayi yafaÉ—i kasa sai ga hawaye sharr, baya nayi na zube kan kujerar dinning nahaÉ—e cinyoyi na na batse, na kifa kai na saman dinning ina cigaba da ba matse cinyoyi na da yuya kai. kuka na fashe da shi da karfi, nashiga bubbuga kan dinning É—in da hannaye na biyu... da sauri ya mike yazo in da nake yana faÉ—in "HAMDAH mene ne me ya same ki?." ban ce komai ba sai kukan dana cigaba da yi, da sauri ya kamo kafaÉ—a ta ya É—ago ni yana cigaba da tambayar abin da ya same ni. jikina nashiga janye wa daga nashi jin kamshin sa ya baibaye ni yana daÉ—a kara min abin da nake ji. yaruko hannuna da kyau ya janyo ni muka dawo cikin parlour, ido ya kuramin yana kallon yan da hawaye ke sauka a idona na sai ya girgiza kai a hankali yace "Kyakkyawa ta me ya same ki?." kai na sunkuyar ina ci gaba da matsar kwalla. a hankali ya janyo ni ya rungume jikin sa ya manna kai na a kirjin sa, wani nannauyar numfashi muka sauke a tare, a hankali yashiga shafa kaina kana yace "Kiyi hakuri HAMDAH amma ki sani wlh shine Allah ina son ki." lamo nayi a jikin sa ina É—an jujjuya kaina cikin kirjin sa cikin mawuyacin hali. sai kuma nayi yunkurin janje kiji na daga nashi jin yanda zuciya ta take ta fizga na izuwa gare shi dan samawa kai na saukin abin da nake ji, da sauri yayi hanzarin mai dani jikin sa, sai kawai nasaki kuka. da sauri ya manna bakin sa kan nawa yashi tsotsa, É“ari jikina ya kama jin yana daÉ—a angiza min wutar fitinar da ke azalzala ta. cak ya É—ago ni yayi da ni cikin bedroom É—ina wan da yake kwana ciki, a kan gado ya dire ni, sai ya zauna gefe na tare da tsura min ido, kana a sannu yaÉ—an rankwafo kaina yace "Kin shirya karÉ“ar bakonci na yau?." ido na rumtse da karfi tare gantsare wa jin yan da jiki na yake wani tsuma tam kar allura ake min. a hankali yakai hannunsa jiki na yashiga shafani, da sumbata ta, a sannu yakai hannunsa izuwa kafaÉ—a ta yashiga murza hannun riga ta yana yin kasa da shi, a hankali yayi kasa da shi har zuwa saman kirji na,É—an sakai tawa yayi a sannu yadawo da hannun nasa kan kirji na dai-dai saman, ababen kirji na ya daÉ—a rankwafofa kai na sosai ya saka yatsar sa guda ya janye rigar tayi kasa nonuwa na suka baina a fili. kai na najuya gefe da sauri, ido ya kafe ababen kirjina dasu yayin da fitar numfashin sa ya karuwa, maganar sa najiyo a sama "Wai da gaske kin shayar da yara biyu a lokaci guda kodai gidan raino kika kaisu?." hannu na yarfe ina murza kafafu na kan katifa, gaba ki É—aya idanuna sun gama rufewa da wutar fitinar da bansan da zuwan sa ba. hannunsa ya sauke su kan nonuwa na. idanuna na rumtse da karfi jin É—umin tafin hannunsa kan ababen kirji na, a hankali yashiga shafa su da matse su, mimmikewa na shiga yi gaba ki É—aya jikina yadaÉ—a amsa wa, babu abun da nafi bukata a yanzu kamar naji sa cikin jikina. da sauri na rirrike hannunsa jin ya shagalta wajen mammatse ababen kirji na, ya É—ago ya zuba min idanunsa da suka gaba canza kala a hankali murya can kasa yace "Ya dai kyakkyawa ta kina marhaban da ni?." ido na rumtse sai ga hawaye shar. kai ya girgiza min da sauri yace "Kiyi hakuri." yafaÉ—a yana zame hannunsa da ga rukon dana yi masa. a sannu naji É—umin bakin sa kan brest É—ina, wani irin bankaro kirjin nayi. billahil azim in da yasan kalar abin da nake ji da bazai zauna yimin waÉ—an nan abubuwan ba, haushin kaina da tsanar yanayin da bansan yan da akayi ya zo min ba ya tabaibaye ni. a sannu yayi kasa da rigar yaraba shi da jikina, yayin da yaci gaba da shafa sassan jikina, zuwa can ya É—ago a galabaice ya zubamin fitinannun idanuwan sa murya a sarke yace "HAMDAH ki na maraba da ni kin shirya karÉ“ar bakwanci na?." wasu hawaye ne masu É—umi suka zubo min ganin bani da mafitar da ya wuce abin da yake nufi, har idan ina son kai na da lafiya. sai na rumtse idanuna tare da gyaÉ—a masa kai hawaye na cigaba da tsiyaya ta gefen ido na. wani murmushi ya sake ya mike jikinsa na É“ari yazare gajerin wando da singlet É—in jikin sa ya haye kaina yayi min rufma. sumbatar fuskata ya shiga yi yayin da hannunsa ke kan ababen kirjina yana ta aikin matse su, kai na shiga yuyawa cikin matsanan ciyar filling, cikin rufewar ido da cushewar Æ™waÆ™walwa naÉ—ago hannaye na na sauke su a bayansa, ido na matse da karfi. najayo sa izuwa jikina. da sauri yashiga karanto addu'a cikin hanzari ya isa da marar sa izuwa nawa, har jikin sa na É“ari, ido na rumtse da karfi jin yanda ya ziyarce ni. wani irin dogon numfashi ya sauke tare da faÉ—in "Washhhhhhhhhhh ahhhhhhhh kyakkyawa ta ashe haka kike shine kika ringa nisanta kan ki gare ni? me yasa kika son haram tamin wannan ni'imar, kyakkyawa ta washiiiiiii aaayyyhhh Allah dai ya saka miki tabbas Allah ya miki baiwa washiiiii Allah wahhhhyyy." wasu irin sambatu yarika yi, yayin da yake nutsu cikin gona ta. numfashi nashiga sauke wa a hankali a hankali, duk da ina cikin yanayin nan amma sai da naji zafi dan ya dage kwarai da gaske yana ta sukuwa kaina, sai dai zafin ma banbanci ne ina jin sa ina kuma jin wutar fitinar da take azalzala ta. sosai ya dage yake kai koma a kaina yayin da yaci gaba da sambatu "Wai da gaske kin taÉ“a aure amma dai bai taÉ“a lumewa in da na shiga yanzu ba, washiii ahhhhyy HAMDAH ina son ki ina son ki I love You I love You, HAMDAH dan Allah ki soni ko rabin yan da nake son kine, na tambata zakici gaba da shayar da ni wannan daÉ—in, wayyooo HAMDAH tai maka ki rike min nan." ya nuna kugun sa da yake sama da kasa kamar zai É“ale. Ya shari tsawon a wa huÉ—u a kaina zuwa lokacin a hankali narika jin abin da nake ji yana raguwa, yayin da wani zafi da mugun raÉ—aÉ—i suka biyo baya, kai na nashi ga juyawa ina shure kafafu na, lokaci guda na nimi filling É—in da nake jin na rasa, kamar a mafarki nake ji da ganin abun, ido na zuba masa ya haÉ—a gumi yayi sharkaf duk da sanyin AC da ke tashi cikin É—akin, yayin da gefen idanunsa ke tsiyayar da kwalla. firgigit nayi kamar wacce ta farka daga bacci. sai na saki kuka ina ture kirjin sa da shishure kafafu kan katifa, cikin Muryar kuka nake faÉ—in "Ka kyale ni ka rabu da ni katashi min a kai wayyo Allah na wayyo zafi, nidai ka rabu da ni." zuwa lokacin bai iya furta komai sai dai idanunsa da ke tsiyayar da kwalla, ta gafe idananun kuma suna rufe. kuka sosai nayi ta yi ina faÉ—in ya kyale ni, amma tamkar baya jina hasali ma idanunsa a rufe suke, sai kuma É“arin da jikin sa ya ke. da karfi ya fizgo wani numfashi sai kuma yashiga sauke numfashin da karfi-karfi yayin da gudun sa ya karu na wasu Æ´an mintoti, zuwa can ya kankame ni kamar zai É“alla ne tare da sakin kara wan da idan mutum yana cikin parlour zai ya jiyo sautin sa.. lamo yayi a kaina yarika sumbatar fuskata, yana mai sauke numfashi a kai a kai... da karfi na shiga ture shi ina faÉ—in "Katashi min a kai nikam ka tashi min a kai." a sannu yazare jikin sa ya kwanta gefe, yana mai cigaba da sauke numfashi. niko cikin takaici da bakin cikin tuno abin da ya faru tun da fari sai nakuma sakin kuka, ina bubbuga kafafu na kan katifa.. a hankali ya mike yaÉ—au gajeren wandon sa ya saka ya mika hannu ya É—ago ni ya rungume jikin sa tare da bubbuga baya na cikin yanayin rarrashi, fizge jikina nayi nakoma nakifa fuskata da jikin katifa, na cigaba da rera kuka na. da sauri yakuma É—ago ni yana faÉ—in "Dan Allah kiyi hakuri ki dai na kukan nan haka, toma wai kukan me kike yi ne iye kyakkyawa ta? kin samar min da farin cikin da ban taÉ“a samin irin sa ba hakika ke É—in ta musamman ce, ban san da wani irin baki zan yi miki godiya ba, amma ki sani kin sanya ni cikin farin cikin da bansan taya zan iya misalta shi ba, Allah ya saka miki da mafificin rahamar sa, yan da kika sani cikin farin ciki da kwanciyar hankali, ya dauwamar dake cikin farin ciki da kwanciyar hankali har abada, dan Allah kyakkyawa ta ki dai na wannan kukan har cikin kasan zuciya ta nake jinsa." fuska ta ya leko tare da sakin wani lallausan murmushi yace "Wai kukan me kike yi ne kam ko bai ishe ki bane na kara." sautin kukan na kara ina tutture shi cikin muryar kuka nashiga faÉ—in "Wlh Allah ban yafe ba ni ka rabu da ni." Æ´ar karamar dariya yayi yace "Baki yafe ba da aka yi me?." "TaÉ“a ni da kayi." na faÉ—a a hatsale cikin sautin kuka. dariya sosai yayi yana daÉ—a kankame ni a jikin sa yace "Ai ni ban taÉ“a ki ba sai da amincewar ki ba ke kika ce nayi ba." dukan kirjinsa na shiga yi ina faÉ—in "Ni ban faÉ—a ba." "Kin mance tun a parlour kike ta jana nazo na baki har a kan gadon nan ma jana kike, dan yanzu kin gama biyan buÆ™atar ki shine zaki ce haka ko." yayi maganar cikin muryar dariya sosai haÉ—e da zallar zolaya yana leko fuskata. kai na tsunkuyar cike da tsananin jin kunya, tuno da abin da ya faru É—azu, tabbas ni kaina nasha mamakin kaina irin yan da nake ji É—azu, tabbas nayi mamakin kai na ba É—an kaÉ—an ba, "Yau wa kin tuna ko to kada ki sake ganin laifi na, ai dama na fada miki sai da amincewar ki zan kusan ceki, ina son ki kyakkyawa ta." baki turo gaba da sauri nace "Ni ka tashi kaje kaje ka kawo min abinci Allah kasa na faÉ—i bazan yarda ba." da sauri ya janyo pillow ya gyara min kwanciya ta kan pillow'n. ya mike da sauti yana faÉ—in "Me kike so kici?." ban amsa shi ba sai yayi waje da sauri. A hankali na mike zaune na É—au riga ta na saka, a sannu na zamo baki. gadon dan fisari ce ta matsani, sai dai ina tsoron na mike kada na faÉ—i, a hankali naÉ—an rika mikewa ga mamaki na sai naga na mike garau, nayi taku É—aya zuwa uku babu alamar jiri ko É“arin jiki tattare da ni. nayi matukar mamakin bana jin ko É—aya daga cikin biyu. kai na jinjina da mamakin karfin jini irin na Ya SALEEM, ban isa ya kusance ni na iya mike wa tsaye da kaina ba har sai na sanya wa cikina wani abu, haka jikina kuma zai yi ta É“ari har sai jinin sa ya gama garwaye jikina... da sauri ya shigo rike da tray yazo ya dire saman table, ya zo in da nake da sauri ya ruko hannuna yace "Zo ga abincin kici kinji." yana kokarin janyo ni, hannu na yarfe nace "Ni fisari zanyi." kafin na karasa faÉ—a ya kinkime ni yayi dani cikin toilet, yana tsaye yace nayi fitsarin kafaÉ—a na make na É“ata fuska nace ya fita. basan sa ya juya yace "To bani ganin ki kiyi." babu yadda na iya dan na matsu sosai. sai da nayi amfani da ruwan zafi wajen yin sarki dan ba karya HQ É—i na yana yimin zafi sosai. ina gamawa yataho in da nake yace "To muyi wanka ko." baki na turo nace "Ka fita." kai ya girgiza kamar karamin yaro yace "Tare zamuyi daga yau har kullum ma." ido na waro kafin na ankara ya É—ago rigata ta kasa ya zare ta a jikina, ya tuÉ“e gajeren wandon sa. duk wani kina da tirjewa ta haka yasa mukayi wankan nan tare. yaso ya É—auko ni ya fito da ni naki fir nace da kafata zan tafi. gaban wardrobe na isa na ciro doguwar rigar bacci har kasa na zura, na É—au pant zan saka yayi saurin matsowa in da nake yarike shi tare da girgiza min kai yace "Kar ki saka." fizge abina nayi ina faÉ—in "Akan wani dalili?." murmushi yayi yana shafa gefen fuskarsa yace "Kika sani ko anjima ki kuma bukata ta." kunya ce ta lulluÉ“e ni ina mai takaicin yanayi na na É—azu. baki na murguÉ—a masa nace "Allah ya sawa ke." dariya yayi tare da rungumo ni cikin yanayin sa na zolaya yace "Allah shi kara dai, zo muje kici abincin kada yayi sanyi." "Ni na koshi." nayi maganar ina ture kirjin sa. yace "Ko É—an tea bazaki taÉ“a ba." nace "Bazan sha ba nace." "To shike nan muje mu kwanta." ido na waro nace "A ina? ni ka rabu dani naje na kwanta." "Yau kam dai ai zaki tayani kwana tun da kin hanani yin bacci da wuri yau, dole fa sai kin sani nayi bacci dan bazan iya yin bacci da kaina ba, tun É—azu nake jin baccin nan kika hana ni yi." ya dago ni cak ya dire ni kan gado, haka yayi ta zolaya ta da jana da wasa, har bacci ya É—auke ni... a ranar kam Ahmad bai iya rumtsa wa ba....👌🻠Washegari bayan ya É—aga ni nayi salla nakuma koma wa bacci, ban farka sai wajen farke 11 na farka, baya cikin É—akin, a hankali na sauka a gadon na shi ge bayi nayi wanka na fito. sai da na saka kaya kafin na isa gaban mirror na zauna, na É—au mai nashiga shafawa a hankali, idanuna ne ya sauka kan wani tablet a kan mirror, a hankali na kai hannu na na É—auki tablet É—in ina bin sa da kallo, da É—inbin mamaki nake bin kwayan da kallo, tabbas komai akayi wannan wayar tana da nasaba da yana yin dana shiga jiya, to me ya kawo shi nan taya akayi kuma na sha. cikin kankanin lokaci nashiga tunano abin da ya faru da ni jiya kafin na shiga yanayin dana shiga daga baya. nagama duk kanin iya tunani na, can tunani na ya tsaka kan yoghurt É—in dana sha tabbas shine abu na karshe dana ci a daren jiya, daga kansa kuma nafara jin yanayin, a hankali nashiga tunanin yan da aka yi na sami yoghurt É—in, a bakin bakin fridge na gani kuma tabbatar ba ni na buÉ—e shi ba, a buÉ—e nagani sai dai murfin yana jikin sa. jin karar buÉ—e kofa ya sani juyo wa ya mai da kofar ya rufe, mai da kallo na nayi kan Æ™wayar kana na kuma duban sa, ido yaÉ—an waro sai kuma ya saki murmushi, ya tako in da nake ya mika hannu zai karÉ“i tablet É—in, da sauri nayi baya da hannnuna ina bin sa da kallon tuhuma nace "Meye wannan?." nayi maganar ina haÉ—e rai. kai ya lankwasar gefe ya janyo ni jikin sa ya rungume a hankali yace "Kada ki zarge ni son ki ne sila." ture kirjin sa nayi nace "So da cuta, kayi amfani da shi wajen birkita min tunani..." da sauri ya rufe baki na da tafin hannunsa ya girgiza min kai a hankali yace "Ko da na saka miki ban yi ba fa sai da amincewar ki, ke kika ce nayi fa...........! 8/19/22, 10:57 - Ummi Tandama😇: *HMDH* *WASA FARIN GIRKI* *NA* *RASHEEDAT S DIRECTOR* 24-45 Littafin na kuÉ—i ne kibiya ki karnta cikin amin ci. part 1 kyauta ne part 2 and wasa farin kirki É—ari 500 kitura ta wannan asusun bankin 3170524141 Rashida Salihu first bank sannan kitura saidar biya ta wannan layin 08034690723 Washegari da asuba kiran wayar sa ce ya É—aga ni a bacci, ko da na É—aga kiran sassanyan muryar sa haÉ—e da yanayin muryar wan da ya tashi a bacci yace "Kyakkyawa ta tashi kiyi salla kinji." kai na gyaÉ—a kamar yana gani na a hankali yakuma faÉ—in "Kin tashi?." cikin muryar bacci nace "Eh." yace "Yauwa to je kiyi salla kiyi mana addu'a sosai kinji." shiru ban amsa ba ina dai sauraran sa in da yaci gaba da faÉ—in "Zakiyi mana ko?." a hankali nace "Eh." "Aha to tashi muje bathroom É—in muyi al'walar tare." yunkurin sa naji na alamun mike wa, a sannu nima na mike na sauko a gadon, maganar sa na juyo yana faÉ—in "Kada ki kashe wayar shiga bayin kiyi al'walar ina ji." baki na turo gaba nace "Ta ya zanyi al'walar da waya a hannuna ka kashe wayar ka ai na tashi." yace "A'a Please Mai kyau ki saka wayar a handsfree ki aje tare nake so muyi al'walar." a hankali na tura kofar bayin na shiga yayin da wayar ke makale a kunne na, na saka wayar a handsfree na ajeta gefen bathtub, na haura saman toilet domin nayi sarki maganar sa na jiyo yana faÉ—in "Wacce irin ruwa zaki zubawa korama ta mai sanyi ko mai É—umi?, sa wayar kusa da shi na ji É—umin sa nayi missing É—in sa sosai." shiru nayi ban amsa shi ba nayi sarki na na mike. a kasan raina nace "Da sanyin nan ne zaka tambaye ni da wani irin ruwa zan yi sarki to ko zafi ake ai bazanyi sarki da ruwan sanyi ba." baki na turo kamar yana gani na na mike tsaye ina kokarin fara al'wala yace "Nace ki saka wayar kusa da shi naji É—umin sa kinji kyakkyawa ta?." "Ni al'wala zanyi." nayi maganar ina kashe wayar, nayi al'walar na fita. kasan cewar babu hijabin da zanyi salla da shi cikin É—akin sai na fita na koma bedroom É—ina, bayan na idar da sallar zamata na gyara na jingina da jikin garu ina azkar. kamar daga sama naji an turo kofa, da sauri na É—ago sai ganin sa nayi ya mai da kofar ya rufe. fuska na É“ata dan naji tsoron yan da aka turo kofar babu ko Knocking. tun daga bakin kofar ya kafe ni da ido, yayin da yake ta ai kamin da wani sihirtaccen murmushi, a sannua ya tako in da nake ya É—an rankwafo kaina sai da ya sumbaci goshi na kana ya É—ago yana yi min kallon cikin ido cikin muryar sa mai sanyi yace "Kyakkyawa ta, ina fata kin tashi lafiya, nayi kewar ki sosai, ki ka hana ni jin É—umin kaya na ta waya ko shiya sa nazo na jisa a zahiri." ido na waro jin abin da ya faÉ—a, yaÉ—ago ni cak yadire ni kan gado, ya zare hijabin jikina. a hankali yashiga sumbata ta yarika bin sassan jikina da kiss yana yi yana shafani da shinshinar jikina, a hankali ya kawo bakin sa saitin kunne na a hankali yaÉ—an ja numfashi ya manna bakin sa jikin fatar kunne na ya sumbace shi tare da faÉ—in "I love You." babu shiri na lumshe idanuna dan har cikin jikina nayi amon sautin sa, sassanyan muryar sa tarika yawo cikin jikina. kokarin ture hannunsa da ya sauke kan ababen kirji na nayi, da sauri ya ruko hannun nawa, murya a cushe yace "A'a kyakkyawa ta ki barni naji É—umin kayana idan kika hana ni kuma sai na shiga in da bakya so É—in." shiru nayi ina jin yan da yake ai kin matse su, a hankali ya manna bakin sa kan nawa, yajima yana sosar bakina yayin da jikina yasoma karÉ“ar sakon sa, a hankali ya zare bakin sa,a tare muka sauke nunfashi. ci gaba da shafani yayi zuwa yanzun kam gaba É—aya jikina ya sake. shiru nayi ina jin yan da yake ai ka min sakwannin sa, nakuma kasa dakatar da shi. nayi mamakin kai na na rashin kara junkurin hanashi abin da yake ta yi a jikina, a hankali yarika janye rigata sama har ya haura da shi saman ciki na, idananu na buÉ—e da sauri jin ya sauke hannunsa kan pant É—ina yana shafa shi haÉ—e da murza shi kasa. cikin hanzarin na rike hannunsa, sai na shiga ture kirjin sa ina faÉ—in "A'a nidai ka bari." hannayena ya rike duka biyu yazuba min ido a hankali cikin fizgar numfashi yace "Ina so naji ya yakwana mu gaisa da shi, nakuma ji É—umin sa bayan shi babu abun da zanyi, idan kuma kika hana ni to tabbas zan shiga na tantance da kyau." ya karashe maganar da kashe min ido. baki na turo gaba nace "Ni dai a'a." hannayena ya matse cikin nasa yayin da ya sanya idanunsa cikin nawa a hankali yace "Please da gaske babu abin da zanyi É—umin sa kaÉ—ai zanji." da sauri na mai da idanuna na lumshe sabo da irin kallon da yake yimin, a hankali ya saki hannaye na. a sannu naji saukar hannunsa kan pant É—ina sai ya rika É—an murza shi kasa, da sauri na yunkura na rike hannunsa, cikin hanzari ya juya hannuna ya rike da É—aya hannunsa yayin da É—aya hannunsa kuma ya janye pant É—in yayi kasa da shi. idanuna na rumtse da karfi, da karfi na mirgina na juya gefe na ja riga ta kasa. Matsowa in da nake yayi ya kwanto jikina, sai ya zura hannunsa ta kasan rigar a hankali ya cusa hannunsa cikin HQ É—ina, idanuna na rumtse jin yan da yake tura yatsar sa da yawo da shi ciki. wani irin gantsarewa nayi da sauri nakuma mirgina wa gefe. "Washiiii Allah kyakkyawa ta bamu gama gaisawar bafa yana kokarin karÉ“ar gaisuwa ta shine zaki raba sakani." da sauri na mike zaune ina daÉ—a jan rigata kasa hararar sa nayi tare da murguÉ—a masa baki. Æ´ar karamar dariya ya sake ya rungumo ni, yana cigaba da dariyar bakin sa ya kawo saitin kunne na yace "Kai kinji yan da rijiyar nan ta kawo ruwa kuwa ko za'a É—an sammin ne in É—ibi ruwan." da sauri cikin matsananciyar jin kunya na kife kai na jikin kafaÉ—ar sa ina cusa fuska ta cikin gefen kirjin sa. dariya sosai yayi ya É—ago kaina yana ci gaba da dariyar, narufe idananuna gam-gam naki buÉ—e wa. cikin muryar dariyar yace "BuÉ—e idon ki kiji wani magana." kafaÉ—a na make ina mai da kaina cikin kirjinsa. shafa kaina yayi a hankali ya furta "Ina son ki kyakkyawa ta, a kullum kamar daÉ—a kara min sonki ake yi." luf nayi a cikin kirjin sa ina juyo sautin bugun kirjin sa a hankali a hankali. wayar sa ce tayi kara a sannu ya mika hannnu ya É—auka, batare da ya É—aga kiran ba, ya leko fuska ta sai ya manna min kiss a goshi. ya É—ago kaina ya tallafe da hannayen sa idananunsa a kan fuska ta yace "Madam zan tafi ki zauna da shirin tarba ta gobe, kiyi tunani ko na seconds ne kinji?." sai ya mike ya sauka a gadon yaÉ—an zuba min ido tare da sakar min sassanyar murmushin sa sai ya juya ya fita. a hankali na yi baya na kwanta jikin pillow tare da zubawa kofa ido, a sannu na maida idanuna na lumshe, amon sautin sa mai sanyi murmushin sa mai taushi laffuzan sa masu taÉ“a zuciya da shiga jiki. su suka yi tayi min yawo cikin ido kwakwalwa da zuciya. a hankali na sauke numfashi tare da mirgina wa gefe na kifu da ciki, tare da yin pillow da hannaye na. daÉ—a lumshe idanuna nayi ina mai daÉ—a lafewa jikin katifa, a sannu wani bacci mai daÉ—i ya É—auke ni..... Da yammacin ranar Ahmad yakuma zuwa sai dai ban bashi dama yayi abin da yake so ba wato taÉ“a jikina, naki barin su Nasmah su matsa ko nan da can, sassanyan murmushin sa da wasu sihirtaccen kallo su yayi ta ai ka min da su, bayan magriba da zai tafi yaruko hannuna yace nazo na raka sa. har munzo bakin kofar parlour yace da su Naseem suyi gudu su riga mu zuwa gurin mota. ai ko a guje sukayi waje, nan ya samu ya rungume ne yayi ta sotsar bakina, sai da ya saukar min da kasalar jiki da ta zuciya kafin ya sake ni yana faÉ—in "I love You!." baya na yi na koma cikin parlour na zube kan kuje ra. shiko a hankali ya juya yana mai sakin murmushin nan nasa yayi waje.... washegari ya kama ranar da zai dawo gidan nan, tun bayan la'asar ya shigo gidan, ina ta É—an zirga zirga na daga kitchen zuwa parlour da kuma sama, kasan cewar yau weekend ne kuma hakan yayi dai-dai da makon karshen wata, duk rana irin ta yau su Zulai suna zuwa duba Æ´aÆ´an su, ganin har yamma tayi basu dawo ba ga shi kuma abinci ya kare su Naseem kuma sai damina suke da suna jin yunwa, shine na shiga kitchen dan girka mana É—an wani abu. duk in da na gilma idanunsa a kai na, daga karshe sai ya biyo ni kitchen É—in wai zai tayani ai kin, na É—auka wasa ne sai naga ya zage muka ci gaba da yi, sai dai idan yaÉ—an yi wani abun sai ya sake ya rungume ni ya kuma yi kissing É—i na a haka a ka gama aikin.... Bayan sallar isha Ahmad da su Naseem ne zaune a parlour'n sama, ina daga cikin bathroom najiyo karar wayata har sau uku ya katse a kuma kira, sai da nagama wanka ta kafin na fito. na isa bakin gado in da wayar ke ajiye na zauna tare da É—aukar wayar, wani kiran ne yakuma shigo wa, da murmushi na gaÉ—a kiran ganin sunan Ukhtee ne ya bayyana kan screen É—in wayar, aje wayar nayi a kan cinyata tare da saka shi a handsfree, nayi sallama. daga cikin wayar Ukhtee ta amsa tare da faÉ—in "Ina yara na?." dariya nayi da faÉ—in "Baki fara tambaya ta ya nake ina lafiya ba shine zaki tambayi yaran ki?, to suna parlour kijira suzo ki tambaye su lafiyar tasu ni bazan faÉ—a ba tun da ni ba a tambaye ni tawa lafiyar ba." tace "Ai bazan tambaye ki ba tun da nima kin mance da ni, Æ´aÆ´ana kuwa na tabbata su basu mance da ni ba, tukun na ma É—azu ne Maama ki faÉ—a min wani batu wai Bappa yake faÉ—a mata wai kinyi aure da gaske ne, so nake ki faÉ—an da bakin ki dan nasan Bappa dai ba zaiyi karya ba." baki na na rufe da hannuna ina dariya kasa-kasa nace "La Ukhtee wai da ma bakuyi maganar da ke ba." tace "Ni tambayar ki kawai nayi da gaske kinyi aure?, so nake naji daga bakin ki." "Yi hakuri Ukhtee afwan nayi zaton munyi maganar nan ai..." da sauri na waigo batare da na karasa faÉ—in abin da zan faÉ—an ba jin an zauna a gefe na, fuska na É“ata dan sam ban san da shigowar sa ba, daÉ—a masowa jikina yayi sosai ya saka hannunsa ya zagaye ni da shi ta baya. maganar Ukhtee na jiyo tana faÉ—in "Ai dama nasan baki damu da ni ba nice kaÉ—ai na damu da ke, ace har kiyi aure ban sani ba in da kin faÉ—a min wlh da zan zo Nigeria, ko kina so kice min bakiyi auren bane kike ta kame-kame." "Wane ita ai aure ba karya bane, nine nan shaidar ki, au bata faÉ—a miki zata yi aure ko tayi bane Ukhtee?." Ukhtee da ta É—an yi dim jin muryar sa sai kuma tayi murmushi mai sauti tace "A'a bata faÉ—a min ba ai bata da kirki, barka da warhaka." yace "Yauwa barka dai, to ayi mata afwa bata laifi ni na amshi dukkan laifin zamu gaiyace ki watarana." tace "To Allah ya nuna mana." yace "Amin amin to mun gode sai da safe." dariya tayi tace "Ya kamar ana kori na?." yace "A'a wai bacci take ji." ya kalleni tare da É—aga min gira da kashe min ido. da sauri nace "Ni ban faÉ—a ba." ai da sauri ya kashe wayar ya sumbaci kumatu na yace "To ni ina ji azo a sani nayi." Da mamaki É—aya zuwa biyu nake lallon sa, kokarin sa na karÉ“ar zancen, da kuma yan da naji ya juya harshen sa izuwa harshen larabci, yana zuba larabci babu ko gargada tamkar Balaraben asali. kumatu na ya ja yace "Kin ki ayi biki kinga gashi an fara cin tarar ki, wace ce ita?." "Jika ce ga masarautar Saudi." na faÉ—a ina kokarin mike wa, yaki bani damar yin hakan ta hanyar daÉ—a rungumo ni jikin sa, yace "Zamu gaiyace ta nan gaba dan ya zama dole ayi biki nan gaba dole waÉ—an da suka halarci taron su sami farin ciki, zan shayar dasu farin ciki kamar yan da kika shayar da ni." a hankali yashiga zame towel É—in jikina kasa, nonuwa na suka bayyana, a sannu ya sauke hannunsa kan É—aya ya matse yaÉ—an sunkuyo da kansa yana kare musu kallo, mike wa tsaye yayi nima da sauri na mike ina kokarin barin gurin naje na sa kaya, sai ya ruko hannuna yazuba min narkakkun idanuwan sa a hankali yace "Ina zakije kuma?." "Kaya zan sa." nafaÉ—a a takai ce ina kokarin zame hannuna yace "To zo kiji wani magana kafin kisa kayan." cak ya É—ago ni ya dire ni kan gado kana yaÉ—an kwanto jikina. nace "Nifa kaya zan sa ka kyale ni naje na saka kaya." a hankali yaÉ—an numfasa kana yaÉ—an É—ago jikin sa ya saka hannu ya zame towel É—in cikin É—an fizgar numfashi yace "Ni na yafe miki kizau na a haka kawai." ya kife tafin hannunsa kan ababen kirji na a hankali Yashiga shafasu da matse su, ido ya lumshe tare da buÉ—e su a kaina wan da tuni suka jima da sauya wa, cikin sixy voice yace "An ya kin baiwa yaran nan nono kuwa? ka da dai ace kin É—au ki hakkin su ki hukuntasu kan laifin da basa da masaniya a kan sa." baki na turo gaba nace "Sai kuma ka gansu haka da lafiyar su, ban yaye su ba sai da suka kai na yaye." murmushi yayi yayin da hannunsa yake kan ababen kirji na yana ta faman matse su a hankali yaÉ—an mike ya rankwafo kaina ya kawo bakin sa saitin nono na yazuro harshen sa, ya lashe kan Brest É—in, wani irin shock ne ya shige ni har sai da na É—an mike tare da gantsare wa, shiko É—an É—ago kansa yayi ya kalle ni tare da É—aga min gira sannan yace "Naga basu yi kama da waÉ—an da aka sha bane." baki na kuma turo, tare da matse idanuna jin yan da sakon sa ya shige ni, a kasan raina nace "Sai aka ce kuma komai sai ka sani ne." "Idan a kan ki ne ba." ido na É—an waro da mamakin fitar maganar tawa. saukar bakin sa kan ababen kirji na naji, yarika tsaotsar su da shafani tun ina É—an tutture shi har na dawo bana ko iya É—aga hannuna sai da ya kashe min jiki gaba É—aya kafin ya É—an É—ago ya zame towel É—in gaba É—aya. ya haye kai na jikin sa na É“ari yashige ni, ban iya yun kurin dakatar da shi ba dan gaba É—aya ya saukar min da muguwar kasala, yayi ta sarrafa ni yana sakin sambatu, yajima sosai yana abu guda ganin kamar bashi da niyyar kyaleni, sai na fashe masa da kuka ina faÉ—in "Ni na gaji." tamkar kukan nawa kai mi yake daÉ—a kara masa, dun dole yayi release, yasulale kai na yana mai da numfashi.. ya zare jikin sa ya kwanta gefe na, duk kanin mu numfashi muke sauke wa, a sannu ya sauka a gadon ya ruko hannuna ya mikar da ni muka shige bathroom a tare mukayi wanka muka fito... yana saka kaya yafita yace zai je yayi wa su Naseem addu'a dan sai da yasa sukayi bacci kafin ya zo nan, bai kuma yi musu addu'a ba. ni ko ina saka kaya gado na haye dan nagaji ga kuma baccin da nake ji. zuwa can yashigo ya haye gadon ya kwanta a gefe na. fuska ta ya leko yace "Kyakkyawa ta akwai kari ne?." yayi maganar cikin zolaya, baki na turo ina kokarin juya fuska ta taÉ—aya gefen. yayi saurin ta ro ni ya matse ni a jikin sa, yayi ta zolaya ta da jana da wasa, har sai da ya sani fashewa da dariya. sai ya tsaya ya kuramin ido yana kallon yan da nake darawa, yaja kumatu na yace "Gaskiya ina da sa'a a rayuwa ta." sai ya daÉ—a rungume ni, ya manna bakin sa kan nawa yayi kissing É—in sa kana ya É—ago, yana yi min kallon cikin ido, kasa jurewa kallon nasa nayi sai na lumshe idanuna.... Washegari da safe haka yaki kyale ni sai da ya sami abin da yake so, wunin ranar kuwa bai leka ko nan da can ba muna tare, sai yammma yaje gidan sa, bai jima ba kuwa ya dawo. akwanaki biyun da Ahmad yayi a gidan nan ya nuna min tsantsar so da kaunar da yake yi min. bayan kwanaki biyun kuwa daya koma yakuma dawo wa, a lokacin yasa zuciya ta yafara yin sabo da shi. ko da ya gama yin kwanakin zai tafi har nake jin bada É—i.... Bayan wani lokaci tuni zuwa wannan lokaci sai da Ahmad ya tabbatar daya dasa wani abu mai muhimmanci a zuciya ta, sai dai sam naki yarda kan cewa so ne, nafi yar da kan sabo ne kawai. a yanzu nakan zauna muyi hira da shi sosai, yanzu har na koya idan ya zolaye ni nima nayi masa, akuma duk san da ya bukace ni nakan amin ce batare da tirjiya ba.... Yau yakama Ahmad zai dawo gida na, tun da yamma na shiga kitchen domin na shirya masa abinci da kaina, dan aduk san da nayi masa abinci da kaina yarka santi da nuna yabawa sai ya daÉ—e yana yaba min. sai daf magriba na gama nashiga wanka, ina fita na na saka kaya na haye kan sallaya, kasan cewar nayi al'wala. bayan na idar da sallah mikewa nayi na je na É—au waya ta, na laluÉ“o number sa, ganin har magriba tayi bai iso ba, iwar haka ai ya daÉ—e da zuwa gidan. har na dannawa number sa kira sai na koma na she, na aje wayar na cigaba da wani da muwa. har aka kira sallar isha nagabatar, har wajen misalin karfe koma saura kwata bai iso ba. sai naji duk babu daÉ—i nakuma ji ina son sanin dalilin daya tsayar da shi har wannan lokacin. a sannu na turawa number sa kira, wayar tayi ta ring ba'a É—aga ba har ta yanke. a hankali nakuma mai da kiran, shima har na fidda ran daga kiran sai na ga an É—aga, shiru na yi banyi magana ba, daga can cikin wayar najiyo muryar Rasheedat tana yin sallama. na amsa sallamar tare da faÉ—in "Ina yini Aunty Rasheedat ya gida." murya É—auke da murmushi tace "Lafiya lau HAMDAH ya yarana suna lafiya, kifaÉ—a musu ranar weekend zan zo na É—auke su." nace To. dariya ta yi tace "Kingan shi shiru bai iso ba ko, kinyi tunanin na rike miki shi ne? to babu ruwa na, in yazo ki titsiye shi ya faÉ—a miki in da yaje yakai dare dan nima yanzu na ganshi, ya dai shiga wanka yanzu, zaki ganshi yanzu insha Allah dan nasan wannan É“arin jikin da yake alla-alla yake ya isa gare ki." murmushi nayi cike da jin kunya nace "A'a wlh nafi zaton yana wajen ne ma." cike da zolaya tace "A'a faÉ—i gaskiya dai." da sauri nace da ita "Sai da safe Aunty Rasheedat." dariya tayi tace "To Allah ya kai mu..........! 25 Muna zaune a parlour muna kallo, har su Nasmah sukayi bacci na kwashe su na kaisu É—aki, sannan na dawo parlour'n na zauna. tun daga step's najiyo takun sa haÉ—e da kamshin sa, da sauri na waigo, karaf muka haÉ—a ido muka sakar wa junan mu murmushi. yakaraso ya zauna kusa da ni tare da sumbatar kumatu na yace "Bakiyi bacci ba." kai na gyaÉ—a sai kuma na turo baki nace "Ina ka je kayi dare?, Aunty Rasheedat tace min ita ma yanzu ta ganka." yace "Zan ce naje gurin wata budurwa ta shine ta rike ni nayi dare." kaina na kawar tare da É—aga hanci sama. yace "In faÉ—a miki tarika miyin daÉ—aÉ—an kalamai shiya sa nayi dare a gurin ta." "Ya isa." na faÉ—a ina mike wa tsaye na sa kafa zan bar gurin, da sauri ya ruko ni ya janyo ni nafaÉ—o jikin sa, sai ya rungume ni. dariya sosai yayi, fizge jikina nashiga yi ina faÉ—in "Ni ka kyale ni ka tashi ka koma gurin ta kaje can kaci gaba da jin zantuka masu daÉ—in." dariya ya kuma yi yace "A'a ina kuma zakije tun bangama baki labarin yadda hirar tamu ta kasan ce ba." kunnuwa na na toshe da hannaye na nace "Bana bukata ka tashi ka tafi kaje kai da kake bukata kaje ka kara ji." da kyau ya daÉ—a rungumo ni cikin muryar dariya yace "Sha kurumin ki Ahmad naki ne ke da Rasheedat kun maye zuciyar babu É—an É—igon gurbin da wata zata samu ta tsugunna, babu wacce naje gurin ta zance babu ita ba kuma za'a yi ta ba, ma'aikatan kamfanunnukan Alhaji na ne muka yi zama da su shiyasa na makara har dare ayi min afwa, ba zance naji ba." baki na taÉ“e nace "Ni ina ruwa na ma idan gurin watan kaje, meye damuwa ta." saida dariyar da yake yayi yazuba min ido kana hankali yace "Akwai ruwan ki da kuma damuwar ki sabo da kina sona, ga kuma kishi na nan cikin idanuwan ki." hannunsa na bige daya kai shi karkashin ido na nace "Babu wani abu a tare da ni kada ma kaga na tambaye ka in da ka tsaya kayi tunanin wani abun ne." yace "Haka ko?, to kalli cikin ido na kice bakya sona, ki kalli cikin kwayar ido na kice bakya sona, oya kalla ki faÉ—a yanzun nan." kawar da kaina nayi na turo baki gaba nace "Ni ka kyale ni." dariya yayi sosai har yana buga kafa ya manna min kiss a kumatu ya É—ago tare da faÉ—in "Aha yarin ya kina wasa, ni É—in fa bana wasa bane jarumi ne ni nan da kike gani." baki na taÉ“e nace "Jarumtar me?." yace "Na iya sace zuciya mana, Allah mai girma yaji tausayin bawan sa mai wahala da dakon so a zuciya da ilahirin jikin sa, ya amshi addu'a ta ya sa miki sona a zuciyar ki, kai gaskiya ni mai sa'a ne." "Waya faÉ—a maka kadai na yaudarar kanka dan na tambaye ka in da ka tsaya, ka laune maganar ta koma wani abu daban, kyale ni natafi na kwanta." nayi maganar ina kokarin zame wa a jikin sa. daÉ—a rungumo ni yayi yashiga zolaya ta,har sai da yasani nayi dariya kana ya É—ago ni cak yayi cikin bedroom da ni..... Washegari yau natashi da kewar ahalina, har da Mama mai awara, ga ba É—aya bani da walwala yau, Ahmad yana cikin É—aki nafito parlour na zauna nayi jugum, tabbas yau ina cikin kewar su sosai, Allah sarki Mama mai awara "Ko tana ina?." nayi wa kaina tambayar, hawaye ne suka ciko ido na Allah sarki wata uwa Mama mai awara, tabbas bazan taÉ“a mancewa da ke a rayuwa ta ba, ke tamkar uwa ce gare ni. ji nayi an dafa ni a hankali na É—ago na zuba masa ido, a sannu ya zauna a gefe na yaroko hannuna yace "Me ke damin ki kyakkyawa ta?." ido na lumshe tare da kuma buÉ—e wa sai na kuma rike hannunsa gam nace "Family na ina jin kewar su, har da Mama mai awara matar data rike ni tamkar Æ´ar data haifa, tayi min gata irin wacce uwa take yiwa É—iyar ta, badun ita ba awancan lokacin da na rasa raina nida abin da suke cikina, ta saida makwancin ta da duk wani abun da ta mallaka tabiya kuÉ—i akayi min CS." hawaye ne suka zubo min sai na yi shiru da maganar dan nasan zan iya fashewa da kuwa. a hankali ya janyo ni jikin sa ya rungume, yashiga share min kwalla yace "Kiyi hakuri babu abin da yake tabbata har idan ya zamo fararre, bagashi yanzu kina bada labari ba, yazama tarihi komai mai wuce wa ne har idan yazamana yana da mafari, kishir ya gobe mukai mata ziyara." da sauri na É—ago da murmushi yayin da hawaye ke ci gaba da sauka a idona nace "Da gaske?." kai ya gyaÉ—a min shima yana murmushi,daci gaba da share min hawaye... bai gushe ba har saida yaga ya sanya ni dariya... Washegari kamar yanda yafaÉ—a motar mu ta hau hanyar Jos, bayan munyi wa su Bappa sallama, kwarai Bappa yaji daÉ—in jin cewa gurin Mama mai awara zamu je, yayi ta zuba mana addu'a da fatan isa lafiya, yaku ce mu gaishe ta sosai da sosai. ni da shi muna gaba Naseem da Nasmah suna baya, dan yaki direba ya biyo mu yace tafiyar family ne dan haka direba yayi zaman sa. da misalin karfe 2 na rana muka iso cikin garin Jos, daga nan nafara yi masa kwatance har muka iso Narkuta, wani numfashi na sauke a bayyane lokacin dana ganni dai-dai kan kwalbatin shigan layin gidan Mama mai awara, nan take tunanin rayuwa ta ta baya tashiga zuwar min, bazan mance ranar dana zo garinnan ba akan wannan kwalbet É—in na zauna har dare, har wasu mutane suka zo amota suna yimin tayin shiga na biyo su, idanuna na rumtse da karfi ina kokarin mai da hawayen da ya ciko min ido. muryar sa najiyo a hankali "Kibar tunanin nan sam bashi da amfani tuna irin haka sai dai ya sanya maka damuwa da É“acin rai, ina zamu bi?." a hankali na buÉ—e idanuna da tuni hawaye ya gangaro min, nayi masa nuni da hannu nace "Mu mike nan." a hankali ya sa kai cikin layin, sai É—an kalle-kalle nake, garin ya canza anyi sabbin gine-gine, nayi ta masa nuni da hannu har muka iso kofar gidan Malam Musa, dakyar shima na iya gane wa dan an yiwa gidan fenti ga kuma sabbin gine-ginen daya zagaye su. kallon sa nayi nace "Ina zuwa bari na shiga na tambayi Zainabu gidan da Mama ta koma sai ta nuna mana muje." kai ya gyaÉ—a, na buÉ—e marfin motar na fita. da sallama nashiga gidan, ga mamaki na wasu mata na gani zaune a cikin gidan suka amsan sallama na karaso ciki, ina ta É—an raba ido ko zan ga Zainabu, na gaida matan suka amsa suna faÉ—in Sannu da zuwa, nace "Yauwa dan Allah Zainabu tana ciki ne?." É—aya daga cikin matan tace "Wata Zainabu?." nace "Matar Malam Musa." sukace "Au wai ai sun jima da tashi a gidanan na sun koma wata unguwar daban." da sauri nace "Innalillahi dan Allah wata unguwar suka koma? ko za'a nuna mana ko ayi mana kwatance." sukace wlh sam basu sani ba, suma haya suke ana gobe zasu tare a gidan su kuma suka bar gidan, sam basu san wata unguwa suka koma ba. cikin sanyin jiki na juya nayi musu sallama na fita, jiki ba kwari na shige cikin motar na zauna duba na yayi yace "Ya dai tayi miki kwatancen gidan ne?." kai na girgiza a hankali nace "Bata nan wasu ne a cikin gidan,kuma wai basu san in da suka koma ba." wasu hawaye ne masu É—umi suka zubo min sai nayi saurin sunkuyar da kaina. a hankali ya dafa kafaÉ—a ta yace "Kiyi hakuri idan da rai da rabo wata rana zaku haÉ—u." kai kawai na girgiza, a hankali ya share min hawayen yace "Ya isa haka na roke ki kada ki sake zubda su ina jin zafin su har cikin dai na, Please na roke ki." ya haÉ—e hannayen sa biyu. kai na girgiza masa a hankali na karasa share hawayen. a sannu yaja motar muka bar gurin. muna fita bakin layin unguwar,na juya da kallo na ta gabar wato hanyar Bauchi, ya lura da hakan sai ya saka hannu ya juyo da fuska ta a hankali cikin tausasshen lafazi da son sama min karfin guiwa yace "Zamuje shima idan Abba ya daÉ—a huce wa." yafaÉ—i hakan ne kawai dan sama min nutsuwa da kwanciyar hankali, a can kasan zuciyarsa sa kuwa bayan Bappa ne sukayi masa ca, "Lallai mutum abin tsoro ne, ka haÉ—a tsihiri da mutuwar ka sabo da kasan duk mai halin irin naka Allah yana musu talala ta hanyar barin su a duniya su shafe shekaru masu yawa, tabbas akwai hisabi ranar gobe kiyama." duban sa nayi jin yaja kwafa afili nace "Ya dai?." kai ya girgiza min da sauri yace "Ba komai ina tunanin tafiyar dake gaban mu ne mukwana a cikin gari kawai, mu huta gobe da safe sai mu juya." nace "A'a kawai mu tafi." ya juya ya dubi su Naseem da tuni suka bingire da bacci yace "Sun gaji kiga baccin su nawa, kema kuma nasan kin gaji." nace "Ni dai mutafi gida kawai." yace "To shi kenan." ya haura hanya muka É—au hanyar Abuja... kasan cewar da abincin mu muke tafe bamu sha wani wahalar yunwa ba, ana kiran sallar magriba muna isa ciki Abuja, yanayin gosulo da muka tarar bamu shiga gida ba sai bayan sallar isha. koda ya gyara parking na buÉ—e marfin motar na fito, ina saka kafata kasa naji wani jiri ya fisge ni, da sauri na dafa jikin motar, har yafita ya zaga yaÉ—au ki Naseem da Nasmah ina dafe da jikin motar, yazo in da hake yana gyara rukon su yace "Muje ko?." a hankali na mike tsawo na yayi gaba nabi bayan sa a hankali ina jin yan da jirin yake ta cigaba da fizgata, a haka muka shiga ciki direct sama ya haura, niko a parlour'n kasa na zube kan kuje ra, tare da kife fuskata jikin pillow'n kujera, na rumtse idanuna da karfi jin juwan nadaÉ—a fisga ta. ya kai su É—akin su ya kwantar da su kana ya sauko kasa yazo in da nake ya zauna kusa da ni. yasa hannunsa ya É—ago ni yana faÉ—in "Shi yasa nace mukwana a cikib Jos sabo da nasan zaki wahala, kika ce sai dai mu juyo, kin ga irin ta ko." murmushin karfin hali nayi dan yanayin da nake jin yana son wuce tunani nace "To baga shi mun dawo ba, ai mun huta basai goben mun yi ta tunanin kuma hawa hanya ba" Yaruko lips É—ina yace "Wannan baki da duk abin da aka faÉ—a sai yakawo hujja". dariya nayi nace "To ai rainon ka ne." shima dariyar yayi yace "Au haka zaki ce." gira na É—aga ina murmushi. gefen fuska ta ya shafa kana ya ruko hannuna yace "Taso na taimaka miki mu haura ki wasa ruwa zaki ji karfin jikin ki." a hankali naÉ—an yunkura ya É—ago ni ya mikar da ni, idanuna na É—an rumtse kana a hankali nashiga É—aga kafata, yana tallafe da ni har muka haura sama. a bakin gado ya zaunar da ni kana ya shiga taimaka min na rage kayan jikina, ya kuma ruko hannuna muka muka shiga bayi wankan ma sai da ya taimaka min gaba É—aya jikina ba kwari ga jirin nan yaki bari na, ga masifaffen ciwon kai. muna fita daga bayin doguwar rigar bacci kawai na zura na haye gado. bakin gadon ya zo ya shafo gefen fuskata a hankali na buÉ—e idona na zuba masa yace "Kyakkyawa ta tashi kiÉ—an ci wani abu mana zaki daÉ—a jin karfin jikin ki." kai na girgiza a hankali na mai da idanuna na rufe, ya hayo gadon ya kwanta tare da janyo ni kijin sa, a hankali bacci ya É—auke ni... can cikin dare jikina yahaÉ—a zafi rau sai É“ari nake,ina daÉ—a shigewa cikin jinin sa, da sauri yabuÉ—e idanunsa ya daÉ—a rungumo ni jin yan da jikina ya É—au zafi yamike da sauri yana faÉ—in "Subhanalla kyakkyawa ta zazzaÉ“i ne haka Innalillahi." gaba É—aya ya ruÉ—e yarika rungume ni yana yimin sannu, ya É—ago ni yana faÉ—in "Taso muje asibiti jikin ki yayi zafi sosai." kaina na kwantar a kirjin sa na rirrike sa a hankali nace "A'a dare yayi sosai kada muje zai sauka zuwa safiya." a ruÉ—e yace "A'a kyakkyawa ta kijin ki yayi zafi sosai muje kawai." duk yan da yaso mu tafi naki fir. yana zaune ina rungumo a jikin sa a haka gari ya waye. da asuba ya kaini bayi da kansa yayi min wanka a daddafe nayi al'wala shima yayi, bai barni na taka da kaina ba ya É—auko ni ya fito da ni, ya shinfiÉ—a mana sallaya a zaune nayi sallar in da shi kuma ya ja mana sallar. muna idar wa na sulale kan sallayar. shiko da sauri ya mike yaje ya É—au wayar sa yakira family Dr su, yace yazo yanzu yayi masa kwatancen gidan. kana yazo ya É—aga ni a kasa ya mai dani kan gado. batare da É“ata lokaci ba Dr ya iso, ya bada umurnin a barsa ya shigo, har cikin parlour'n sama ya bashi umurnin shigo wa, kana ya shigo ya saka min hijabi kan rigar baccin da yake jikina, ya É—ago ni ya tallafo ni jikin sa muka fito parlour, ya zaunar dani kan kujera kana shima ya zauna kusa da ni, a hankali na kwantar da kaina jikin hannun kujera, ina jin Dr yana tambayar me ya sa me ni, yace masa tafiya mukayi jiya mun wuni a kan hanya,muna dawo wa shine zazzaÉ“i ya rufe ta. Dr ya É—anyi rubuce-rubuce kana yaÉ—a go yace "Baza a bata magani ba sai anyi mata test." Ahmad yace "To." kana ya dube ni yace "Bari a ja jinin ki ayi test dan asan maganin daya dace da kisha ki warke da wuri ko kyakkyawa ta." yayi maganar yana É—an jan hijabin jikina ya É—an tattaro shi yaciro hannuna ya ruko hannuna. Dr ya taso yaja jinina kana ya tafi. in da aka ja jinin yarika mulmula min a hankali, shiru nayi ina kwance cikin kirjin sa, a haka bacci ya fara fizgata, ganin haka sai ya gyara zaman sa da kyau ya gyara min kwanciya ta cikin jikin sa. nan da nan bacci ya É—au ni... Acikin baccin narika jin magana, a hankali na buÉ—e idanuna, maganar Dr ne ya doki kunne na "Congratulations ranka shidaÉ—i an sami karuwa Madam tana É—auke da juna biyu." wani irin waro idanuna nayi na mike zaune. Ahmad kuwa mike wa tsaye yayi zumbur yana bin likitar da wani irin kallo mai cike da É—in bin mamaki cikin rawar murya yace "What! mekace!?, kasan me kake faÉ—a kuwa?." sai kuma ya girgiza kansa sannan yace "Kodai kunnuwa na sun jiye min ba dai-dai bane." murmushi Dr yayi tare da mike wa tsaye takar dar dake rike a hannunsa ya mika masa yace "Wannan shine sakamakon test É—in da mukayi, kuma ya nuna tana É—auke da ciki, amma idan ana kokonto za'a iya zuwa wani asibiti ayi gwaji ta hanyar yin scanning domin tabbatar wa." takardar da ya mika masa yashiga dubawa har hannunsa na É“ari, wani uban kabbara ya sake, ya juya ya dubi gabar yasulale kasa yayi sujjada............! Kuyi hakuri na rashin jina kwana biyu kanwa ta ce tayi É“ari so dole nice na zauna a kanta na tsawon kwana É—aya da wuni É—aya ban sami damar hawa online É—in bama bare na shaida muku. Mommyn Twins ce 8/19/22, 10:57 - Ummi Tandama😇: 26 Ya É—ago tare da É—aga hannunsa sama yace "Ya Allah ya Ubangijin rama Allah nagode maka Nagode maka Allah, ya buwayi gagara misali ya Hayyu ya Kayyum, bana da tsumi bana da dabara maikowa mai komai duk kai kaÉ—ai kake da su, haki Ubangiji na mai girma ka azirtani da abin da bana da wayo da wayo da ikon iya bawa kai na, duk arziki na bazan iya baiwa kaina ba kai kaÉ—ai kake da ikon iya bani, Allah Nagode maka Allah na gode maka Allah Nagode maka." yakuma mai da kansa yayi sujjada, yana mai cigaba da kwararo addu'a da kirari wa Allah. kana ya É—ago da sauri yamike yazo ya rungume ni tsam yana faÉ—in "Hakika HAMDAH ke alkhairi ce a gate ni, ke fitala ce mai haske duhun dayayi shekara da shekaru, na gode wa Allah daya mallaka min ke amatsayin mata kuma fitila ga rayuwa ta, HAMDAH ke ta daban ce ina sonki ina sonki HAMDAH inayi miki son dayafi wanda nakewa kaina!!." yadaÉ—a kankame ni a jikin sa. Dr da yake tsaye yana bin mu da kallo da murmushin taya murya, yayi mana sallama yace zai tafi, ai da sauri Ahmad ya sake ni yace ya bashi account number É—in shi, nan take yayi masa transfer É—in 3 Miliyan. yace tukuicin sa na sanar da kyakkyawan zance mafi girma, wan da tun da yake ba'a taÉ“a yi masa albishir da kamar saba. likitar yarika murna dayi masa fatan isowar baby lafiya ya bar gidan bakin sa har kunne, bayan ya aje mana maganin da yazo da shi. Ahmad daya kasa zaune ya kasa tsaye yara inda zai sa kansa dan farin ciki, yadube ni yana faÉ—in "Me kike so kyakkyawa ta me kike so a duniyar nan? kifaÉ—a min ko mene ne shi ashirye nake nayi miki shi koda zai zamo gurfaniwar dukiyar dana mallaka da dukkanin kadarori na, me kike so nayi miki tukuici da shi? motoci gidaje kamfanoni acikin kasar mu ko a kasashen waje, faÉ—a min duk abin da kike bukata zanyi miki shi koma mene ne, faÉ—a min yanzu kyakkyawa ta." kai na rausayar gefe jin kai na nadaÉ—a sara min a hankali cikin yanayin jin zazzaÉ“i nace "Ni bana son komai wayyo kaina." na dafe kaina dake cigaba da sara min. da sauri ya mike yace "Bari na É—auko ruwa kisha magani zai dai na in sha Allah." da sauri yaje ya É—auko gorar ruwa cikin fridge yadawo in da nake, ya tsiyaye ruwan cikin cup É—in da ya haÉ—o da shi, kana yaÉ—au laidar maganin ya curo su daga cikin laida, kamar yadda yagani a rubuce haka ya cicciro su. kana ya tallafo kaina yace "BuÉ—e bakin ki na saka miki." da sauri na kawar da kaina yayin da naji zuciya ta ta hautsune jin warin maganin nace "A'a zanyi amai." yace "Ya ilahi bazakiyi ba, buÉ—e baki kisha ga ruwa nan kusa." cikin zubda kwalla na girgiza masa kai da faÉ—in "Zan yi mana kabar shi kawai zan warke a haka basai na sha magani ba." ido ya waro da karfi ya furta "Wane ni wlh ban isa ba, kin san kuwa zafin zazzaÉ“i yana iya zubda ciki, ki tai make ni dan Allah ki ceci rayuwa ta kisha maganin nan ki samu ki warke kada ya janyo min babban asara, na roke ki dan Allah ki sha, ki taimaka min ni kaÉ—ai iyaye na suka haifa ki tai make ni abin cikin nan yafito lafiya, naji a raina inada jinina aduniya." ya juyo da fuskata yace "Sha in Allah ya yarda bazakiyi amai ba." idona na rumtse da karfi na É—auke numfashi tare da buÉ—e baki ya zuba min maganin kana ya bisu da ruwa. da kyar sai da nayi kamar ina yi kafin suka wuce. ido na ware da karfi jin zuciya ta na wani irin tashi cikin hanzari na tallafe kansa tare da manna bakina da nashi nashiga tsotsar bakin sa. a hankali a hankali nashiga sauke numfashi, yayin da aman yake kwanciya a hankali. sai na lumshe idanuna a hankali ina mai cigaba da tsotsar bakin sa, a hankali kasan tuwar mu da Ya SALEEM a irin wannan lokacin yafara zuwar min, sai na buÉ—e idanuna da sauri a sannu na zare baki na daga nashi. shiko ido yakura min da yanayin mamaki sai kuma ya tallafo kaina yana kokarin kuma haÉ—e bakin mu. da sauri na kwace kai na na turo baki gaba,nace "Bana ce maka zanyi amai ba." murmushi yayi yace "To baga shi kin mai da aman ba, zo in kara kwantar miki da shi." kafada na make ina mai cigaba da turo baki gaba. da sauri ya mike cikin rawar jiki yace "Ina zuwa bari naje na sanar wa su Bappa wannan dadda É—an albishir É—in." ido na waro nace "A'a kada kaje." kafin na rufe baki ma yayi gaba. A kofar side É—in su Bappa ya haÉ—u da shi yana kokarin fita. ganin yan da yake ta washe ba yasa Bappa faÉ—in Ahmad "Wannan farin ciki haka me ya faru." cikin matsananciyar farin cikin daya ke jin kansa ciki yace "Bappa Malam HAMDAH tana da ciki, yanzu likita ya tabbatar min da haka." Bappa ya faÉ—aÉ—a fuskarsa da annuri yana faÉ—in "Masha Allah Allah abin godiya alhmdllh Allah mun gode maka, kai lallai wannan abin farin ciki ne, Allah ya É—aiyiba yaraba lafiya." Inna Wuro dake ta ciki tana jiyo duk abin da suke ciki, tayi murmushi mai bayyana farin ciki, ta girgiza kai tare da faÉ—in "Yaran zamani kenan wai shi ya É—auki kafa yazo faÉ—ar matar sa na da ciki." takuma yin murmushi tana faÉ—in "Dole kayi murna Ahmad lallai wannan abin farin ciki ne." Anan kofa kuwa Bappa yayi ta zuba musu addu'a da fatan isowar abin dake cikin duniya lafiya, yajuya cike da É—in bin farin ciki, shiko Bappa ya koma ciki, yana shaida wa Inna Wuro. tayi dariya tace "Ai duk ina jin ku murna ya hana shi sukuni." Bappa yace "Ai dole yayi murna abune sabo a gare sa wan da ya jima yana sumayar sa sai gashi kwasam Allah ya ai ko masa da shi, kin ga kuwa dole farin cikin sa yagaza É“uya." tace "Haka ne kam lallai muma munyi farin ciki kwarai aure yayi albarka." Bappa yace "Haka ne kuwa kwarai da gaske." haka sukayi ta nuna farin cikin su da sam barka da fatan isowar baby duniya cikin koshin lafiya... Ahmad kuwa yana juyawa daga gurin Bappa Rasheedat ya kira a waya ciki farin ciki yasanar mata, ihun murna Rasheedat ta sake tace "Ina HAMDAH haÉ—a ni da ita dan Allah." yace "To bari na kai mata." ai bata jira ya karasa maganar ba ta kashe wayar da sauri ta zari matafin ta da makullin mota tayi waje. Ahmad yana tafiya yana daddanna wayar sa nan da nan yashiga posting wa Æ´an uwa da abokan arziki, yana faÉ—in a taya shi murna.. Ina kwance a kan kuje ra in da ya barni yadawo ya same ni, ya karaso in da nake da sauri ya sunkuyo ya sumbaci goshi. ido na lumshe tare da buÉ—e su a kan a hankali nace "Yanzu kaje ka faÉ—a musun ne?." baki ya washe yace "Eh mana ai dole duk wani wan da ya sanni yasan wannan labarin." ya zauna ta gurin kafafu na kana ya É—ago kafafun nawa ya É—aura su kan cinyar sa, a hankali yashiga matse su. yana faÉ—in "Sannu kinji kyakkyawa ta baki dai kin ciwon ciki ko?, iya ciwon kanne kaÉ—ai?." ban tanka shiba sai lumshe idanuna danayi.. kira yayi ta shigo wa wayar sa yana É—agawa yana faÉ—in yagode yagode, gaba É—aya bakinsa yaki rufuwa... Acikin Æ´an mintina Rasheedat ta iso gidan tana haurowa parlour'n sama ta taho da gudu ta rungume ni daga kwancen da nake, cikin sananin farin ciki tace "HAMDAH kai sannun ki da kokari ashe dai zamuga jinin mu Allah ya fito mana da shi lafiya." ta mike ta sauri ta rungume ta Ahmad tana fadin "Aboki wayyo Allah narasa yadda zan sa kaina dan farin ciki, tabbas yau ya daÉ—a yarda Allah bai mance da mu ba." dariya yayi yana daÉ—a rungume ta a jikin sa yace "Kwarai kuwa Kawa Allah baya bacci." Haka suka yi ta nuna farin cikin su kamar zasu saka ni cikin jikin su. suka rika tambaya ta me nake so, Aunty Rasheedat tace me nake jin kwaÉ—a yin sa ta dafa min. nace ba komai. kan kace me labari ya karaÉ—e yan uwa da abokan arziki. ranar wuni Aunty Rasheedat tayi a gidan sai dare ta koma. washegari washegari da sassafe Ahmad yaje gidan su, yau Æ´an gidan sun sha mamakin ganin yan da yashigo da farara hatta Sakeenat yau sai da ya amsa gaisuwar ta. É—akin Hajiya Karima ya shige, tana ganin sa ta faÉ—a fuskar ta da murumshi. ya nimi guri ya zauna bayan sun gaisa ya dube ta fuska É—auke da masananciyar farin ciki yace "Hajiya wani albishir nazo miki da shi." zama Hajiya Karima ta gyara ta washe baki tana faÉ—in "To Ahmadu É—an Sabil na bada goron kar É“ar albashir fari soll." yace "Hajiya HAMDAH nada ciki Hajiya ashe nima zan haihu?." wani irin zabura Hajiya Karima tayi, sai da ta zamo bakin kujera ta buga kirji ta waro ido tare da faÉ—in "Me ne ciki!!?." wani irin murmushu yayi mai kunshe da ma'anoni daban-daban kana yace Hajiya kema kin ji abin a bazata ko? ai nima haka naji abin kamar almara." dariyar yake tayi sai kuma ta kama kame-kame tashiga faÉ—in "La..laa..ikon..Ikon.. Allah...to ciki.. ciki, kai masha Allah lallai kuwa wannan shine bazata bayan fidda rai ga samu sai ga samun kuma, kai amma nayi farin ciki naji daÉ—i sosai, ashe zanga jika na, kai Allah yayi albarka yaraba lafiya, Eh Allah ya raba lafiya." "Amin amin." yafaÉ—a yana mike wa tsaye yace "To Hajiya ni zan koma." tace "To a gaida gida a gai da min me cikin." yace to kana ya sa kai ya fita.. yana fita Hajiya Karima ta saki wani uban ajiyar zuciya tabigi kirji tace "TabÉ—ijam ciki!? kenan hakan na nufi Ahmad zai haihu yasami magajin dukiyar sa, wato wannan shigiyar yarin yar tana kokarin zuguza min shiri shine har da yin ciki, bayan ban taÉ“a kawo hakan cikin lissafi na ba, nasawa raina bazai haihuwa ba shine zata zo ta yi kokarin haihuwa masa, ina bazai yiwu ba da sakel wlh!...." Acan cikin garin Bauchi Abba ne da Ummi tafe cikin mota a hanyar su na komawa gida bayan dawo war su daga asibiti dubiyar wata Æ´ar uwar Ummi da ba lafiya, suka biya ta gidan mai domin su sha mai, tun daga farkon shiga gidan man layi ne har cikin gidan man, Abba da yake kokarin sako kan motar sa cikin gidan man yaÉ—an yi jim yana bin layin da ido. Ummi tace "Abba'n Fauzan wannan layin idan muka shiga ai sai mukai kisan dare ma layin bai iso kan mu ba, duba fa gamasu garaku da suke acikin motoci sannan ga su motocin kansu, yaushe za'a basu har a bamu." Abba yace "Gaskiya kam bari mu koma gida kawai nasa direba yafito ya sha man ko ba a nan ba, tun safe ake layin nan motoci sai daÉ—a zuwa suke zamu É“ata lokaci kam muje gida kawai." Ummi tace "To in ban da mutane ma ga wasu gidajen mai da yawa waÉ—an da naga babu ko layi wasu bai fi mota biyu zuwa uku ba, baza su je can susha man ba sai suzo nan suyi tayin layi haka." Abba yace "To ai sauki ake so shiyasa ake wa gidan man layi, ai ba nan kaÉ—ai ba idan da zaki zaga garin nan kiga gidan mai me irin sunan wannan gidan man zakiga layi kamar haka koma fin haka, man su na da sauki sosai kuma litar su na da kyau, an ce wai mai gida jen man ne tace a rika sai da shi a farashin da yanzu suke sai dawar shiyasa duk gidajen man ta zakiga irin wannan layin." kai Ummi ta jinjina ta É—aga kan ta tana duban sunan gidan man. tace "*HAM'NAS CO PETROLEUM NIGERIA LIMITED* wato mace ce mai gidan man?". Abba daya juya akalar tafiyar tasu izuwa gida yace "Eh mace ce." tace "Lallai tayi kokari Allah yasaka mata." Abba ya amsa da amin amin. suna isa gida motar SALEEM na shigo wa, w kusan tare sukayi parkin suka fito, ya tako ya zo in da suke ya shiga gaida su, suka amsa cike da kuwala Ummi taÉ—an zuba masa ido nan da nan ta hango Æ´ar karamar ramar da yayi, ta dube shi da kyau sannan tace "SALEEM baka da lafiya ne kam?." kai ya girgiza batare da yayi magana ba. tace "Ai ho nazaci baka da lafiya ne dan naga kaÉ—an faÉ—a kaÉ—an." Abba yace "Wata kila hidimar office ce ta sashi a gaba kin san shima yana sa haka idan ka rasa nitsuwar ka." Ummi tace "Haka ne Allah yasa mu dace." suna nan tsaye motar Abbu yashi gidan, koda ya gyara parking yafito duk kanin su gaishe sa sukayi ya amsa, in da ya amsa gaisuwar SALEEM a sama-sama kana yayi gaba Abba ya bi bayan sa. SALEEM kuwa motar sa ya shige yabar idan, Ummi kuma ta wuce side É—in ta. Parlour'n da su Abbu suke zama suÉ—an tattauna nan suka wuce, suka zauna suna É—an tattauna lamuran su. Abbu ne yamai da hankalinsa kan TV yana sauraran labaran almuru da ake gudanar wa a wannan lokacin, in da ake sanar wa kan manyan masu kuÉ—i da suke bada taimako da tallafi ga marasa karfi, jinjina kai yayi jin ta in da taimakon ya fito yace "Kai wannan matar Allah dai ya saka mata wlh tana da kokari sosai, ko wancan satin ma naji kalar taimakon da tayi na dubban nin É—arurruwan kuÉ—i ga mara sa karfi, in dai za'a cigaba da samin irin su a Nigeria ai kasar mu zata cigaba ba É—an kaÉ—an ba, dubi yan da take ta bada mai kamar kyau ta a cikin gari Allah dai ya kara mata buÉ—i." Abba ya amsa da "Amin amin ai Yaya ko yanzu ma bakaga layin da ake yi a gidajen manta ba irin su kuma kullum buÉ—e suke gani ba ci baya ba." Abbu yace "Kwarai da gaske Allah ya daÉ—a buÉ—a mata." hirar suka cigaba da yi har sai da aka kira magriba kafin suka nufi masallaci. bayan sallar isha da Abbu ya tafi side É—in Mamie hirar matar yayi ta mata da irin kokarin da take, sukayi ta sanya mata albarka da dukiyar ta.....) Abuja Zaune muke a parlour ni da su Naseem Aunty Rasheedat tayi sallama da kaya niki niki a hannun ta, Zulai da Talatu na biye da ita É—auke da wasu kayan, ta Suka dire shi sakiyar parlour, na dube ta daÉ—an mamakin ganin ta da manyan laidadi nace "Sannu da zuwa Aunty Rasheedat." tace "Yauwa HAMDAH ya nauyin jiki?." murmushi kawai nayi dan nidai bana jin wani nauyin jiki cikin da bai girma ba ake tambayar nauyin sa. zama tayi gaban kayan kana ta shiga ciro su cikin manyan laidodin kayan baby ne kala-kala a ciki haÉ—e da kayan wasa, da gudu su Nasmah suka je in da take Naseem daya É—ago wani abin wasan baby yace "Mamy kin kawo mana ne?." Kuma tun sa ta ja tace "A'a zan kawo muku naku wannan na baby'n ciki ne, baku san Mommy zata samo mana yaro ko yarin ya ba." tsalle sukayi cike da murna suna faÉ—in "Yeee Mommy zata samo mana yaro." Nasmah ta dubi Aunty Rasheedat ta dafa kafa É—ar ta tace "Mamy yaushe Mommy zata samo mana?." yatsun ta shida ta nuna mata tace "Saura wata haka ta samo nama." tsallen murna tayi tazo in da nake da gudu tace "Mommy guda haka zaki samo mana yaro." ido na waro ganin ta É—aga yatsun ta biyar tana yimin nuni da su nace "Akuya ce ni." dariya Aunty Rasheedat da Talatu da Zulai sukayi, Talatu tace "Ai ba akuya kaÉ—ai suke haifan biyar ba idan Allah ya nufa sai kiga an haifo biyar É—in." kai na girgiza nace "Ba amin ba wlh." dariyar suka kuma. Aunty Rasheedat tace "Muna so ko goma ne ma Allah yakawo su masu albarka." ido na kuma waro wa ina faÉ—in "Lallai ma." ÆŠakin kayan wasan su Naseem tasa su Sulai suka kwashe kayan da tazo dashi, suka kai cikin É—akin suka jibge shi a gefe. Bayan wata É—aya.........! Mommyn Twins ce 8/19/22, 10:57 - Ummi Tandama😇: 27 Tun daga ranar da Ahmad yasami labarin ina da ciki, bai sake barina nayi wani abu da kaina ba. ko wan ka baya bari na nayi shi yake yi min da kansa, ko naki nace ya bar ni nayi da kai na sai ya ce bai isa na janyo masa a sara ba, shi da kan sa zai min. koda six yake da ni a hankali yake bi da ni. tun da Dr ya bashi shawarwari game da cikin kan abincin da zan rika ci,sabi da lafiya ta da ta abin da ke cikin. shike nan ya hana ni sakat da cin abinci. a rana sai yabani naci abinci kusan sau goma, dan yanzu idan ya bani naci anjima kaÉ—an zai kuma kara min. yanzu kullum muna tare da shi ko yana gida na ko baya gida na, idan yana gidan sa da sassafe zai zo bazai koma ba kuma sai dare. washegari kuwa zai kuma dawowa da sassafen... Kwance nake a kan dago na tasa É—an karamin ciki na gaba wan da yanzu watan sa huÉ—u kenan. idan bama kasan da cikin ba, bazaka ce da wani halitta cikin cikina ba, dan bai wani fito sosai ba, bakamar irin cikin su Naseem lokacin da ya kai watanni huÉ—u ya fi sosai kamar wan da yafi watan nin sa ba. Ahmad ne ya shigo É—auke da plt a hannunsa, perpesun kayan ciki ne haÉ—e da ganyen ogu da dafeffen kwai a gefe, wanda yasha kayan kamshi da na yaji sai tashi da kam shi yake, ya dire plt É—in saman table kana ya hayo gadon ya zauna ya tankwashe kafafun sa a gaba na yashafo fuskata yace "Kyakkyawa ta taso kici perperun gashi na É—ebo miki." fuska na É“ata nace "Ni na koshi ba É—azun nan ci ba, ni bana jin yunwa yanzu." ido ya waro yace "To ai ba sai kinji yunwa ba, bakiji abin da Dr yace ba kirika cin abinda zai kara miki jini da kuzari da lafiyar baby na ba ga perpesun can cikin tukunya ko kwata baki ciba, kuma yanzu nasa Zulai ta kuma girka miki gwaten wake da hanta." ido na waro nace "Nayi yaya da shi sauran perpesun ma kaje ka basu su ci ni nagaji da ci, kullum-kullum kawai mutum yayi ta ci." yace "Dan Allah ki taimake ni kitashi ki ci,cin waÉ—an nan abubuwan fa sune samin lafiyar ki data baby na, so kike a sami wata matsala? dan Allah ki tashi ki ci kada yayi sanyi." ya saka hannu ya É—ago ni, ya tallafo ni ya ware kafafun sa ya sani sakiyar cinyar sa, kana ya mika hannu ya É—au plt É—in yasaka shi gabana, ya É—ibo perpesun a cokali zai kai bakina. karÉ“i cokalin nace "Ni zan ci da kaina." yace "To ci maza dan Allah ki cinye duka." nace "To Allah kaÉ—an zan ci dan bana jin yunwa." yace "To ci dai." a hankali nasoma ci, ganin na fara ci sai ya daÉ—a gyara zaman sa da kyau, a sannu ya tura hannunsa cikin riga ta ya kife hannunsa kan ciki na, wani nannauyar ajiyar zuciya ya sauke a hankali yashiga shafa cikin. bai fi cokali biyar na ciki ba nace nakoshi. da sauri yace "Please kyakkyawa ta kiÉ—an kara kaÉ—an." nace "Allah nifa na koshi." duk yan da ya matsa kan na kara ko kaÉ—an ne naki daya masa sai na sa masa kuka, ai da sauri ya rungume ni yashiga rarrashi na.. Washegari tun da sassafe ya É—aga ni da kyar na buÉ—e idanuna dan bacci ne fal a ciki, yace "Tashi muje kiyi wanka mutafi asibiti yau zaki fara awu, dan likita yace cikin na cika wata huÉ—u yakamata ki fara yin awu kin ga yau Monday dai-dai kenan." fuska na É“ata nace "Ni bacci nake ji kabari ba yau ba." da sauri yace "A'a ina, duk da dai baccin da awun duk suna da amfani amma dai muje a duba lafiyar baby in mun dawo sai ki cigaba da baccin kinju kyakkyawa ta." ya karashe maganar da tsi gar rarrashi. kai na gyaÉ—a masa a hankali. murmushin nan nasa mai narka zuciya ya sakar min kana ya sauke bakin sa kan goshi na ya manna min kiss, idanuna na lumshi tare da kuma buÉ—e su, ya É—ago yana kallon fuska ta a hankali ya furta "Ina son ki kyakkyawa ta." idanuna na kuma lumshe wa a lokaci guda na buÉ—e, tabbas na gama yarda da son da yake yimin a koda yaushe ina hango sona acikin kwayar idanunsa. idanunsa cikin nawa cikin sanyin murya yace "Yaushe zaki faÉ—a min kema kina so na da bakin ki?." kasa nayi da nawa idon batare da nace komai ba. murmushi yayi yace "Ko a iya haka ma na gode." duban sa nayi da fuskar tambaya jin ya faÉ—in haka. murmushi ya kuma tare da É—aga min gira kana yace "A faÉ—a min É—in ne dai ajin ya hana amma gashi nan ina hango shi." yasa yatsar sa karkashin idanuna. kai na nayi saurin kawar wa tare da yunkurin mike wa, Æ´ar karamar dariya yayi ya taimaka min na mike tsaye yayin da ya soma zolaya ta. "Ajin nan ya ishe ni haka a ajiye shi a gefe a fito fili a faÉ—a min ana sona, tun kafin ajin ya tsinke dan wata jiya ta tare ni a hanya tace tana sona, nace ta bari tukun da wan da nake so idan bata ce tana sona ba zan zo na amshi soyayyar ta." baki na taÉ“e dan yanzu na gama karantar kalar zolayar sa nace "Ayya ai da ka amince mata kawai." da sauri ya leko fuska ta yace "To ai ke nake jira Æ´ammata idan baki faÉ—an kina sona ba sai na koma gurin ta." "Yi maza kaje ka sanar mata kada ka maka anan." nafaÉ—a ina kokarin wuce sa, da sauri ya ruko ni yace "Bari dai na É—an kara jira tukun." ya janyo hannuna muka shiga bayi. bathtub ya cika da ruwa mai É—umi, kana ya tuÉ“e min kayan jikina, na shige ciki na zauna ina mai jin daÉ—in ruwan, na lumahe idanuna. da sauri na buÉ—e idanuna jin motsin sa cikin ruwan sai ganin sa nayi shima a tuÉ“e, ya É—au sosa da sabula yashiga wanke ni shima yana wanke jikin sa a haka akayi wanka, kana ya ruko ni muka fito bedroom, koda nazo sa kaya hana ni yayi sai da yagama sumbatar ciki na kafin ya saka min da kan sa. muna gama shiri muka fito muka dadda an gama wa su Naseem shirin School. a saman dinning duk muka yada zangon mu, sai da ya haÉ—a musu abincin da duk sukace suna so kafin ya juyo kai na. perpesun naman zabbi ya zuba min haÉ—e da tea mai kauri yana kokarin zubo wani abun nace masa ya isa wannan É—in ma ba iya cenyewa zan yi ba. ciki na ya shafo yace "Yanzu fa zaki fara kamata yayi ki fara da mai yawa." duban su Naseem yayi yakamo kumatun su yace "Kanin ku yakusa isowa Yaya Naseem da Aunty Nasmah." washe baki sukayi cike da jin daÉ—i Naseem yace "Daddy ina kanin?." ciki na ya shafa yace "Ya na nan yakusa fito wa." da sauri Nasmah ta mike tazo kusa da ni tana kokarin jan riga ta sama. hannunta na bige nace "Ke meye haka?." tace "Mommy danga kanin ne fa." fuska na É“ata nace "Ka dani ko." dariya yayi sosai kana yaÉ—an sakaita dariyar, ya dafa kanta yace "Zaki gan shi?." kai ta gyaÉ—a tana washe baki. yace "To ba ri ki ganshi." juya kujerar da nake yayi yadurkusa kana ya saka hannu yana kokarin jan rigata sama, nayi saurin rike hannunsa nace "Me ye haka?." juya hannun nawa yayi yarike cikin nasa kana yajan je rigar da É—aya hannunsa, yace "Kibar yara suga É—an uwan su." tafin hannunsa ya kife kan cikin yana É—an shafawa yace "Nasmah zo ki gani ga kaninku a nan yaron yana nan a nan." dariya sukayi har suna rige-rigen taÉ“a cikin. Naseem yace "Daddy ni ban ganci ba." yace "Yana cikin ciki yakusa fita ku ganshi." sallen murna suka yi suna faÉ—in "Ye damuga yaro, Mommy data samo mana yaro." kafa na shiga bubbugawa a kasa nace "Kuma na fasa cikin abincin." da sauri ya saki rigar yace "Yi hakuri kyakkyawa ta ci mu tafi o." sai da yayi ta lallami na kafin na soma ci. hannu ya saka muka ci tare muna ci yana karawa da dabara yayin da yake ta jana da wasa har naci da yawa sosai. bayan mun gama muka fito waje in da Talatu ke biye da mu rike da school bag É—in su. ko da akazo shiga mota dirjewa yaran sukayi suka ce sam moton Daddy'n su zasu shiga, fuska na É—aure nayi musu tsawa nace "Maza ku shige kusha mota kutafi so kuke kuyi latti." da sauri yace "A'a a'a kyale su kushiga muje, Talatu sa musu jakar su cikin mota." da sauri tace to. ya buÉ—e musu motar suka shiga, Talatu saka musu jakar su cikin motar, kana ya buÉ—e min nima na shiga, ya zaga gefen direba ya shiga ya ja motar, mai gadi ya buÉ—e get muka fice a gidan.. sai da yafara bi ta makarantar su da kansa ya sauka ya ruko hannunsu ya shiga da su cikin makarantar kafin ya fito muka nufi asibiti. Muna shiga cikin asibitin batare da É“ata lokaci ba aka gama kimsa mana komai, koda nazo shiga É—akin awu tare da shi muka shiga, yana tsaye yana kallon komai, idan yaga nurse É—in taÉ—an danna cikin sai yace wai tayi a hankali kada a sami matsala, a haka a ka gama muka fito muka nufo gida. Tun daga lokacin idan wata ta zagayo lokacin zuwa awu yayi da shi muke zuwa kuma yana tsaye za'ayi komai.... Haka rayuwa yaci gaba da tafiya, sosai Ahmad ke kula da ni baya kaunar yaga wani damuwa ko É“acin rai tare da ni, bazai taÉ“a samin sukuni ba har sai yaga ya gusar min da damuwa ya sanyani farin ciki.... a yanzu cikina watan sa 7 yafito É—as da shi, haka zai tasani gaba ya tuÉ“e min riga yayi ta kallon cikin, yana ganin in da yake motsa wa, yayi ta sumbatar sa, idan nace ni na gaji ya kyale ni. sai yace ai ba da ni yake ba da babyn sa yake, wai yana mika masa gaisuwa.... Zaune nake a parlour Inna Wuro tashigo rike da manyan kofuna guda biyu, ta iso ta dire su a gaba na tazau na nata faÉ—in "Sannu HAMDAH ya nauyin jiki." murmushi kawai nayi. É—aya kofin ta buÉ—e ta miko min tace "KarÉ“i kisha maganin zaki ne dana bayamma zai taimaka miki sosai." nace to na amsa nasha da É—an yawa ta karÉ“a sauran ta mika min É—ayan shima na sha. ganin Ahmad ya shigo yasa ta mike wa tana faÉ—in "Anjima ki kara sha shi zai zamo ruwan shanki za'a kawo miki wani anjima." nace to ya karaso ya gaishe ta ta amsa tana fita daga parlour'n. ya zauna gefe na tare da É—aga riga ta sama ya sumbaci cikin kana ya É—ago yana faÉ—in "Mene ne Innar ta kawo miki shine ba tayi." nace "ÆŠauka ka sha." buÉ—e marfin kofin yayi yaÉ—an kai bakin sa ya É—an É—ana yayi saurin aje kofin yana yamutsu fuska. dariya na yi nace "Ka kara mana." yace "A'a ya ishe ni, amma meye wannan É—in?." nace "Maganin zaki ne da na bayamma." yace "Meye su É—in." nayi masa bayani ta yanda zai fahimta. yace "Oh to karÉ“a ki kara sha, ai naji tana cewa anjima ki kara sha shine ruwan shan ki." fuska na É“ata tare da make kafaÉ—a nace "Ba yanzu nasha ba." yace "To an jima kaÉ—an zaki kara." nace "To kabari anjiman yayi mana." yace "To ai gara dai na tuna miki tun yan zu kar anjiman yayi kice da saura." dariya nayi ina faÉ—in "Ai irin anjiman ka ne yanzu sai kace yayi." shima dariyar yayi yace "To shike nan a saka time kada lokaci yayi kice bai yi ba." nace "Eh a saka." yace "Bayan minti 5." "Tab banyar da ba yayi kaÉ—an." "To na kara biyar a kai." nace "Naki wayon." yace "To ashirin yanzu kam ba kankari." Ai kuwa duk bayan minti 20 zai sani na sha, ganin ya matsa min sai na gudu sashin su Inna Wuro. har can É—in ya bini da kofunan yace wa Inna Wuro ta kara maganin wannan ya kusa kare wa. nace "Allah Inna Wuro kar ki kara ni nagaji da sha tun É—azu yake ta bani." yace "Ina ance yazama ruwan shan ki ne." "Shike nan shan ruwan babu adadi ni ciki na zai fashe." Inna Wuro tayi dariya tace "Idan ta shanye wannan da rana sai dare kuma sai a kawo mata wan da zata sha har gari ya waye." nan ne ya kyale ni amma yace mutafi na karasa shanye sauran. nace ya tafi zan zo anjima, fir yaki sai da ya tasani gaba muka koma... tun daga ranar kullum shi yake zuwa da kansa ya karÉ“o min ruwan maganin, yakuma tasa ni gaba sai na sha... A bangaren Hajiya Karima kuwa tsaye take ita da wasu maza guda hiyu, a cikin bedroom É—in ta, sunyi jungum-jungum kamar waÉ—an da aka aiko wa da bakin labari, É—aya daga cikin mutanen yace "Hajiya shima kawai a kunce masa tayar mota yabi uban sa inda yaje." Hajiya Karima tace "Ai matsalar ba daga nan take ba, yanzu fa duk wata shirin mu ya kwaÉ“e idan aka kashe Ahmad tofa anyi ba'ayi bane, dan kuwa yanzu yasami magaji dole a mufara bi ta kan ita matar tasa mai cikin kafin shi." É—ayan yace "To Hajiya me kike ganin za'ayi mushiga cikin dare mu harbe banza kawai." tace "Ina ai bazai yiwu ba dan gidan ta da matakan tsaro iri-iri, akwai jami'an tsaro da masu gadi kuma ko wannen su yana da bindiga, shigan gidan zai bada wuya, dole dai mubi ta wata hanyar, ni a tuanani na kawai mu jira ta haifi cikin sai mu kawar da shi,in yaso duk mu haÉ—a har da ita mai azarÉ“aÉ“in yin cikin kafin shi Ahmad É—in. suka ce haka za'ayi, nan suka cigaba da tattauna in da lamarin zai tafi musu batare da wata matsala ba..... A gurguje Please 👌🻠Bayan wata biyu Yau tun da gari ya waye nake jina wani iri, sai dai narika daure wa ban nuna masa komai ba. har wajen karfi sha É—aya, zuwa lokacin kam nafahim ci nakuda ce kuma sosai nake jin sa. har kuma lokacin ban nuna masa wani abun na dami na ba na rika daure wa har mukayi wanka yafita, kafin yafita kuwa yayi ta tambaya ta, babu abin da yake damu na me kuma na ke so. nace masa babu komai... ina zaune a bakin gado nayi nayi na iya mike wa na kasa, sai na zame kasa nasaka goiwowi na a kasa na kife kaina jikin gado, ina juya kai cikin mawuyacin hali. "Innalillahi'wa'inna'ilaihirraji'un wayyo Allah na." nafaÉ—a da karfi ina juya kai. sallamar Faty naji daga bakin kofa, da karfi na É—aga murya na kira ta, da sauri ta shigo nace "Je ki kira min Inna Wuro da sauri." hankali tashe ganin halin da nake ciki ta juya da gudu tayi waje. ina ji ana kiran waya ta har ya kase ban iya É—auka ba, har sau uku kiran na katse wa sai a na huÉ—u da kyar na mika hannu na janyo wayar, na É—aga kiran tare da saka shi amsa kuwa, muryar Ahmad naji yana faÉ—in "Kyakkyawa ta kina lafiya ya baby na?, hello kyakkyawa ta bakya jina ne." wani irin hurÉ—a cikina yayi haÉ—e da baya na da sauri nakai hannuna na safe baya na tare da faÉ—in "Wayyo Allah wayyo Allah Innalillahi'wa'inna'ilaihirrraji'un." cikin wani irin birkitaccen murya yace "HAMDAH me ke faruwa me ya same ki me nene!!?." salati kawai na cigaba da yi batare da na iya furta komai ba, jin yan da ya birkice yake ta tambaya ta sai na janyo wayar na kashe... Inna Wuro ta shigo hankali tashe, ta iso in da nake tana faÉ—in "Ikon Allah abun yazo kenan sannu HAMDAH Allah ya raba ku lafiya." ta dubi Faty tace "Je ki ce wa Zulai ta É—aura ruwa a wuta, ki wuce kije É—aki na ki É—auko hulba cikin magungunan nan ki kawo mata ta zuba cikin ruwan ta girka, ta É—ura cikin flaks, yi maza yanzun nan." da sauri tayi waje. Inna Wuro ta shiga karanto addu'a tana shafa min a cikin da bayan da nake ta kukan sa... ya turo kofar kamar wan da aka jefo sa da sauri haÉ—e da sassarfa ya iso in da nake ya rungumo ni yana faÉ—in "Innalillahi'wa'inna'ilaihirraji'un sai da na tambaye ki ko dawa matsala ce kafin na fita kika ce ba komai, meyasa zaki barni na tafi, tun É—azu jikina ya bani akwai abin da yake faruwa da ke shiyasa nakasa samin sukuni kan abin da nake, ya zaki min haka HAMDAH, sannu kyakkyawa ta sannu kinji." cikin sananin azabar nakuda na kankame rigar sa ina faÉ—in "Wash wash wayyo Allah wayyo Allah na wayyo baya na." Inna Wuro kam waje tayi da sauri, zuwa can ta shigo rike da kofi da hulba mai zafi ciki, har lokacin yana rike da ni a jikin sa. ta mika masa cup É—in tace "Bata tasha wannan insha Allah zai zo mata da sauki." da sauri ya karÉ“a har hannunsa na É“ari, tace "Bata da zafin shi." ya zauna ya mike kafafun sa ya saka ni sakiyar cibiyoyin sa, kana yasaka min cup É—in a baki na yana faÉ—in "Sha zaki haihu yanzu." Inna Wuro ta sake fita da sauri ta koma sashin su, É—akin Bappa ta shiga yana zaune rike da Æ´ar karamar kwarya a hannunsa yana ta tofe ruwan maganin dake ciki da addu'a, yana ganin ta ya mike da sauri yace "Ya dai?." tace "Har yanzu dai." kwaryar ya mika mata yace "Kai mata tasha insha Allah zai ta kai ta." ta karÉ“a ta fita da sauri. a in da ta barmu a nan ta tadda mu, da kan ta ta maso ta kafamin kwaryar a baki tace nasha da bismilla. sai da na shanye duka kafin ta É—aga kwaryar. tana yimin sannu. wani irin zabura nayi nan take wani gumi yashiga tsastsafo min ta ko ina yashiga É“ari a jikina, yayin da cikina yashiga murÉ—a na ba ko kakkautawa. kai kawai naje juyawa yayin da nakasa iya furta komai. a zabure ya mike yaÉ—ogo ni cak yana faÉ—in "Inna Wuro mutafi asibiti kawai." kan tace me yayi waje yana isa gurin motar sa ya saka hannu ya buÉ—e gidan baya yasaka ni ciki, Inna Wuro ta karaso da É—an sassarfa tashige motar ta zauna gefe na. da sauri ya shige gidan direba yaja motar da mugun gudu ciki. hanzari mau gadi ya wangale get yasa kai da mugun gudu. tamkar zai tashi sama haka yake sharara gudu batare da É“ata lokaci ba muka isa cikin asibiti, yana kashe motar yafito da sauri yazago gefen da nake yabuÉ—e ya cicciÉ“o ni, yayi dani cikin asibitin, Inna Wuro tabiyo bayan mu, nurse's suka nuna masa É—akin da zai shiga dani, ya wuce ya dire ni kan gado cikin É—aga murya ganin Nurse's É—in sun rufu a kaina yace "Kuje ku kira likita mace tazo ta duba ta." nan da nan ma'aikatan sukayi waje batare da É“ata lokaci ba Dr mace ta shigo nurse's biyu na biye da ita. duk yan da sukayi ya fita yabasu guri domin su gudanar da aikin su sam yaki, da kyar ya yarda ya fita ya tsaya daga bakin kofa yana leka ni. wani irin nishi na sake tare da faÉ—in "Innalillahi'wa'inna'ilaihirraji'un." dai-dai nan kan É—an yasoma kunno kai, ai da gudu ya shigo ya rirrike ni ganin yan da hawaye ke zuba min yace "Sannu HAMDAH kiyi hakuri ina sonki." kai na jujjuya tare da rike hannunsa da karfi, nace "Wayyo Allah na zan mutu." likitan tace "Kada ki dai na nishin ci gaba." ai bata rufa baki ba sai ga É—a yafito fut tare da calla kara. nurse tana kokarin É—aukar sa ya ture ta ya É—auke sa ya rungume a jikin sa yana faÉ—in...........! Mommyn Twins ce 8/19/22, 10:57 - Ummi Tandama😇: 28 Yana faÉ—in "Masha Allah Allahu Akbar ya iso duniya! É—ana ya iso!!." yawani sake rungume shi yana juye cike da matsanancin farin ciki mara misal tuwa. da sauri Dr ta mika hannu ta karÉ“i É—an dake ta faman calla kara tace "Yi hakuri ranka shidaÉ—e bari a gyara shi, gashi ka É“ata jikin ka da jini, kaÉ—an bamu guri mu kimsa shi da mamarsa zamuyi mata É—in ki wannan katon É—an naka ya karata dole sai munyi mata É—inki." kai ya girgiza yana daÉ—a leko fuskar yaron da ta ke kokarin mikawa nurse. niko numfashin wahala nake ta sauke wa a raina inayiwa Allah godiya daya raba ni da cikin nan lafiya. matso ni yayi gaba É—aya bakin sa yaki rufuwa ya damke tafin hannuna cikin nasa yace "Sannu kyakkyawa ta Allah dai yayi miki albarka." kai na rausayar gefe ina mai cigaba da sauke numfashi wahala. kiss ya sauke min a goshi kana ya juya yafita sabo da maganar da likitar ta sake yimasa kan zasu fara É—in ki... ya fito yana ta washe baki, jama'a sai kallon sa suke ganin yan da yafito jikin sa duk jini, da sauri Inna Wuro ta iso in da yake tana faÉ—in "Ahmad ya haka ya jikin ka da jini." baki ya daÉ—a washewa bai damu da jinin dake jikin sa ba cikin sanananin tarin farin ciki yace "Inna Wuro ta haihu kin ga babyn kuwa bakiji kukan sa ba?." dariya Inna Wuro tayi tana faÉ—in "Masha Allah Allah abin godiya, Allah yaraba su lafiya." Ahmad yakasa zaune ya kasa tsaye bakin sa yaki rufuwa, mutane kuwa sai daÉ—a kallon sa suke da jikin sa da ya É“aci da jini, da yan da bakin sa ya kasa rufuwa. suna ta shan mamaki wai haihuwa aka yi masa yake ta irin wannan farin cikin. wayar sa ya É—aga yana ta daddanna wa yama rasa wazai kira ya faÉ—a masa abin farin cikin nan. Rasheedat yakira ya sanar mata. ai ko batare da É“ata lokaci ba ta iso asibiti da katon akwati, kayan jarirai ne tam ciki, da sabbin jiga-jigan dogayen riguna masu tsadar gaske, da sauran abubuwan bukata wacce mai jego da baby ya kamata suyi amfani da shi idan akayi haihuwa. ta bawa nurse tace a je a shirya baby, da maman baby, suna shiga da akwatin. ta rungume Ahmad tana tsallen murna. suna tsaye aka fito da jaririn an shiyar sa cikin tsadadden saiti cikin wan da Rasheedat tazo da shi, har ana rige rigen karÉ“ar sa sakanin Ahmad da Rasheedat da kuma Inna Wuro. Karshe wa Rasheedat aka mika mawa dan gaban su ta wuce tariga mika hannu. nurse É—in tace "Muna tayaku murna an sami É—a na miji." Rasheedat tace "Wayyo Allah masha Allah kawo shi kawo shi." tana karÉ“ar babyn ta ciro kuÉ—i masu yawa É—aurin Æ´an 1-1k cikin jakar ta ta mika wa nurse É—in da ta fito da yaron. tace tikun cin ta na sanar da abin da aka samu. da sauri Ahmad yace wa nurse É—in "Ya take tana lafiya dai babu wata matsala ko." tace "Eh babu komai yanzu za'a wuce da ita É—akin hutu." kai ya jinjina. Rasheedat ko ido ta kurawa yaron cike da matukar farin ciki da É—oki tace "Wayyo Allah kyakkyawan yaro, wannan yaron da ala kama da ni zai yi." dariya Inna Wuro tayi tana lefo fuskar yaron tace "Tabatakallah masha Allah wannan katon yaro haka duk kai kaÉ—an ka ka baje cikin kicin nan haka." Ahmad yasaki dariya mai nuna zallar farin ciki ya mika hannu yace "Kawo sa na gansa É—azu ban gansa da kyau ba." Rasheedat tace "Amma yanzu zaka bani shi ko?." kai ya gyaÉ—a mata yana dariya, ta mika masa É—an daya ke ta rarraba ido kamar ba yanzu yafito duniya ba, idan haske yaÉ—an dame sa sai ya rufa idon yakuma buÉ—e wa. ido ya kura masa babu ko kiftawa sai daÉ—a washe baki yake, yarika sumbatar yaron yana kuyi cike da shauki mai bayyana zallar jin daÉ—i da farin ciki.. dakyar ya mika wa Inna Wuro shi tana karÉ“ar sa Rasheedat takuma caÉ“e shi. a hannun Rasheedat yayi ta wa yaron hotuna a wayar sa, cikin kankanin lokaci yawatsa shi wa duniya, batare da É“ata lokaci ba yafara É—aga kiran yan taya murna.. sun so shiga su duba HAMDAH aka dakar da su akace tasami bacci su bari sai ta farka da kanta... duk da haka Ahmad a akai-akai yake shiga É—akin hutun da aka kai ta yana duba ta.. Sunan a cikin asibitin har wajen karfe uku, gaba É—ayan su babu mai gajiya bare jin yunwa. sai a lokacin wata nurse tazo tace musu ta farka zasu iya shiga yanzu. ina zaune a kan gadon da aka kwantar da ni, bayan Nurse ta taimaka min na shiga bayin cikin room É—in wan da yake a tsaftace, nayi wanka da ruwa mai É—umi na kimsa jikina, ta ciro min É—aya daga cikin dogayen rigunan da Aunty Rasheedat ta kawo su cikin akwati, na fito fes dani kamar ba ni bace É—azu nake a hargetse, ina zaune ina shan maltina da madarar da nurse's suka kuma haÉ—a min, su Ahmad suka shigo. wani sassanyan murmushi ya sake min tun daga bakin kofa. fuska na É“ata na turo baki gaba. suka karaso ciki suna yi min sannu, Inna Wuro tace "Sannu kinji Æ´ar nan Allah ya raba lafiya sai fatan samin sauki kuma, Allah ya kara miki lafiya." murmushi kawai nayi mata. da sauri Ahmad ya amsa da amin amin. Rasheedat ta maso bakin gadon tace "Sannu HAMDAH sannu da kokari yaya jikin dai?." itama murmushin nayi mata a hankali nace "Da sauki." wani irin murmushi yakuma sakar min tare da kashe min ido, yaÉ—an matso ya rike hannuna ya matse cikin nasa yayin da ya gyara rukon babyn da É—aya hannunsa, a hankali cikin sassanyan murya mai É—auke da zallar farin ciki yace "Madam kinga kyakkyawan yaro na kuwa." baki na murguÉ—a masa nace "Baka tambaye ni gajiyar wuyan da ya bani ba sai ta tashi ma kake ko." da sauri yace "Sorry kyakkyawa ta na isa gaisuwa ta ta musamman ne." yayi maganar cikin yin kasa da murya sosai tare da kashe min ido. da sauri na zare hannuna cikin nashi ganin hankalin su Rasheedat ya dawo kan mu. yana rungume da yaron a hannunsa sai leka fuskarsa yake Inna Wuro tace "Ahmad kawo shi a kwantar da shi, yan zu zai bukaci kwanciyar tun É—azu yake hannu." yace "A barshi dai zuwa anjima sai a kwantar da shi kamar bacci zai yi ma yana rufe ido." kai Inna Wuro ta girfiza tare da yin murmushi tace "Ai yayi baccin yafi a kirga yana farkawa a ganiye yake shi kansa yana bukatar hutu, kada jinin sa ya daÉ—a masa tsami." sai da ya sumbaci goshin yaron kafin ya mika mata shi ta kwantar da shi gefe na, sai a lokacin naga kalar fuskar yaron, kato fari soll da shi kyakkyawa mai kama da ubansa hancin dai nawa ne, dan kalar hancina ne zane a kan fuskarsa, numfashi na sauke a raina nace "Ka gama wahalar da ni." Da misalin karfe huÉ—u likitan ta shigo ta É—an dudduba ni bayan tambayoyin da tamin ko akwai abin da ke damu na, nace mata ba komai. tace zamu iya tafi tun da babu wata matsala tare da ni. bayan magungunan da ta rubuta tace a siya narika sha... Rasheedat ta É—auki jaririn shi kuma ya taimaka min muka fito, Inna Wuro na janye da akwatin muka isa jikin mota, ya buÉ—e min gidan baya na shiga, kana ya karÉ“i a kwatin yasaka shi a but, Inna Wuro ta shiga ta zauna kusa da ni, ya zaga mazaunin direba in da Rasheedat ta zauna a gefen mai zaman banza tana rungume da jaririn. a sannu ya ja motar a hankali muka bar cikin asibitin... Muna isa gida da sauri ya fita ya buÉ—e min kofa ya ruko hannuna na fito daga cikin motar. tuni ma'aikatan gidan maza da matan su suka hallaro in da muke, suna yi mana sannu da tambaya ta ya jiki dakuma barka da samun baby, suka rika rika leka fuskar yaron dake hannun Rasheedat suna sambarka da faÉ—in Allah ya raya. ganin ina yamusa fuska yadube ni cike da kulawa yace "Kin gaji ko muje ki huta." yajanyo hannuna muna É—an yin nesa da inda suke ya É—aga ni cak yayi cikin side É—in nan da ni. bai dire ni ko ina ba sai cikin bedroom É—ina a kan gado. yaÉ—a go yana bina da wani irin kallo mai cike da tarin so da kauna, a hankali ya kawo fuskar sa daf da nawa, a sannu ya haÉ—e bakin mu. wani zazzafar kiss yake ai ka min da zafi-zafi kana ya zare bakin sa yana mai cigaba da yimin wannan kallon, sai kawai ya rungume ni sam a jikin sa, yace "Hakika bani da bakin da zan iya yi miki godiya amma ki sani ina sonki ina kaunar ki ke alkhairi ce a rayuwa ta." sai ya sake ni ya É—ago jin hayanir su Rasheedat a parlour. Inna Wuro ne tashigo da salla Rasheedat na biye da ita... nan da nan Inna Wuro ta shiga kiciniyar yiwa yaron wanka, guri ya nima ya zauna yana zaune har aka fara yi masa wankan, jin yana kuka da ganin yan da Inna Wuro take wanke shi yasa shi faÉ—in "Inna Wuro ko dai zafi yake ji?." dariya tayi tace "Har ma yasan daÉ—in jikin sa kenan, ai ko dole a wanke shi sosai acire masa dattin da ya fito da shi." shiru dai yayi yana kallon sa da alama dai ransa bai yi daÉ—i ba. bayan an gama masa an shirya sa cikin wani sabon kaya tuni ya yi bacci cike da jin daÉ—in wankan da aka masa. yaso ya É—auke sa ganin yana baccin ne dai ya hakura ya fita.. Rasheedat ma tafita taje gurin su Talatu da suke kitchen. Bayan Inna Wuro ta kwantar da shi tace na tashi muje nayi wanka.. wankan towel tayi min sosai nasha zafi kam amma bayan an gama naji daÉ—in jikina sosai. Rasheedat ta shigo É—auke da tray mai É—auke da kayan abinci kala-kala, masu in ganta jiki, Inna Wuro ta sani na zauna naci da zafi-zafin sa. ai ko ina saka kaya nima na haye gado sai bacci... Da daddare bayan ya maida Rasheedat gida, yadawo yashigo É—akina yazauna bakin gado ya É—au jaririn yana ta kallon sa. Inna Wuro ta shigo ta kuma fita ganin yana cikin É—akin, da kyar na sashi yafita dan nasan so take ta kwanta dan tayi shin fiÉ—ar ta a kasa a gefen gado.. washegari Bappa har parlour'n sama ya hauro, Inna Wuro ta kai masa yaron yayi ta masa addu'a da sanya wa rayuwar sa albarka, kana nafito muka gaisa yana tambaya ta ya jiki bana dai jin ciwon komai ko, nace ba komai, yace "Masha Allah akwai manin da bawa Innar ku zata girka miki kirika sha." nace "To Nagode Bappa." ya mika min É—an yafita, namike na koma É—aki.. nakira Ukhtee na faÉ—a mata na haihu gudun kada taji a wani gurin tace ban faÉ—a mata ba. Ukhtee tarika murna tace insha Allah zata zo Nigeria da ita za'ayi suna... Ahmad ne yashigo rike da su Naseem a hannunsa yana ce da su "Au bakuga yaron bane?." kai suka gyaÉ—a masa suna washe baki. murmushi nayi ganin su, É—azu Inna Wuro take cemin sun shigo jiya ina bacci ita ta hanasu tada ni. gado suka É—ale dukan su har da shi, ya É—auki yaron yana faÉ—in "To ga kanin ku nan yafito duniya kuzo ku ganshi." tsallen murna suka shiga yi suna faÉ—in "Yeee Mommy ta samo mana yaro." Naseem yace "Daddy kabani shi na rike shi." yace "To gyara ka zauna na baka shi." ya zauna har da tankwashe kafafu, yasaka masa yaron kan cinyarsa yana rike da shi batare da yasake masa shi ba.. Nasmah ma tace itama sai dai a bata, ya É—ago shi itama yasaka mata shi kan kafarta. murmushi nabisu da shi ganin yan da suke ta murnan ganin yaron. Ahmad ya dube ni yana faÉ—in "Ya dai kyakkyawa ta komai normal ko." baki na turo nace "Ba kun sami baby kun share ni ba." ido ya waro yace "Wane mu ai kece tauraron mu bakya taÉ“a disashe wa." murmushi nayi shima murmushin ya bini da shi. A É“angaren Hajiya Karima lokacin da labarin haihuwar nan ya isketa hankalin ta yayi mummunar tashi, Musamman da aka ce mata na miji aka haifa, awani É“arin zuciyar nata kuma shirin da suka haÉ—a kan kawar da É—an ta tuno a fili tace "Lokaci yayi." a shirya taje gidan Inna Wuro ta fito mata da jaririn, ta kafe shi da ido tana dariyar yake da faÉ—in Allah ya raya.. Ranar da muka cika kwana uku da safe bayan Inna Wuro tayi masa wanka muka shiga bayi nima tayi min, bayan mun fito na shirya cikin riga da zani na atamfa, ina zaune a bakin gado ina cin abinci, yayin da jaririn ke rike a hannun Inna Wuro. Ahmad ya shigo, ya leka fuskar yaron yana gai da Inna Wuro, ta amsa da murmushi tana faÉ—in "Gashi nan ai yana so yaji abibcin sa cikin baki, gara dai kabar ta itama ta ci dan ka samu ruwan nono mai yawa." murmushi mai sauti yayi yace "Kodai bai sha ba tun É—azu shiyasa yake nima." tace "A'a kam wannan acicin yanzu aka cire shi daga bakin nono shidai yafi son ko da yaushe ya kasan ce a bakin ci." hannu ya mika ya karÉ“e shi yana É—an jijjiga shi, ya dube ni yana faÉ—in "Madam ayi sauri a ci a bashi yasha dan Allah, Allah sarki ga yana buÉ—e baki yunwa yake ji." baki na turo nace "Ai nima yunwar nake ji." yace "To ai ke babba ce zaki fishi dau riya." cikin shagwaÉ“a nace "To Allah sai na fasa cin abincin kuma bazai sha." ido ya waro yace "Asara biyu kenan, yi hakuri ci abincin ki ni bari na rarrashe shi." kasa Inna Wuro tayi da kansa cikin yanayin shiga jin kunya. ya juya yana faÉ—in "Inna Wuro bari ayi masa huÉ—uba." tace "Yakamata kam yau yau uku." yayi waje rike da shi yashige É—aya É—akin da ke kusa dana su Naseem.. har na kammala cikin abincin bai dawo da shi, Inna Wiro ta fita tace bari taje tayi wanka, niko na gyara na kwanta har bacci yafaraÉ—a É—auka ta kafin ya shigo. a hankali ya hayo gadon yace "Yi hakuri kyakkyawa ta tashi ki bashi nono kin ji, Allah yunwa yake ji kiga fa sai latse baki yake." na mike zaune tare da karÉ“ar sa dan nasan yanzu kam yana bukatar nonon sosai. kiciniyar janye rigata sama na shiga yi, sai ya maso ya taimaka min yaja rigar sama, yasaka hannun sa cikin bra ta ya ciro nonon da kansa ya saka masa shi cikin baki niko naÉ—an tallafe masa saboda kada yayi masa nauyi a baki. ya sunyar da kansa ya sumbaci saman nonon, kana ya É—ago ya saka hannu ya ciro É—ayan, a hankali ya manna bakin sa ya sumbace sa shima, yace "Nayi missing É—in ku." sai ya saka hannu yarika shafa nonon, a sannu ya leko fuskar yaron yayin da hannunsa ke manne kan É—aya nonon yace "Yau wa sha sosai ka kara kato." murmushi nayi tare da duban sa nace "Wani suna ka saka masa ne?." baki ya washe yace "AHMAD." ido na waro nace "Wane Ahmad fa kace Ahmad kuma." yace "Eh Ahmad sunan da yanzu nayi masa huÉ—uba da shi kenan." kai na jinjina nace "To me za'a rika ce masa kenan?." yace "Babu wani sunan da za'a rika kiran sa dashi face sunan sa Ahmad Ahmad Tijjani Sabil." baki na rike nace "Taya za'a rika kiran sa da Ahmad bayan sunan ka kenan ai sai a nemo wani sunan da za'a rika kiran sa da shi." yace "A'a kyakkyawa ta sunan da za'a kira sa da shi kenan asalin sunan sa Ahmad." baki na turo gaba nace "To har yara ma haka zasu rika kiran sa da shi?." murmushi mai sauti yayi kana yaja kumatu na yace "To ai su yara basu ma san sunana ba kuma ko da ace sun sani ma nasa daban ne nawa daban, bare ma basu sani ba Daddy kaÉ—ai suka sani, sai dai idan kece zaki faÉ—a musu." da sauri nace "Yaushe." kumatu na yakuma ja yace "Duk san da kika cigaba da kira na da sunan." nace "To ba sunan ka ba kenan Ahmad." ido ya waro tare da yin dariya yace faÉ—ar sa bai miki nauyi a baki ba, ko da Ahmad karami kike?." kai na sunkuyar ba shakka sunan tayi min mugun nauyi, yauce rana ta farko tun farkon haÉ—uwar mu da shi har rana mai kamar tayau ban taÉ“a kiran sunan sa kai tsaye ba sai dai narika yin komai a dungu, bana taÉ“a iya kiran sunan sa. hannu ya saka ya É—ago haÉ“a ta yace "Me kika ce sake faÉ—a naji ni Ahmad É—in?." kai na daÉ—a sunkuyar wa ina murmushi, ai ko ba komai shi babba ne, hakan baya rasa nasaba da rashin iya kiran sunan sa da nake kai tsaye, ko ba komai ya girme min nesa ba kusa ba, ga wata babban girman wato da yake a matsayin miji na. fuska ta ya leko yace "To in ba so kike ki sanar musu da sunan nawa ba, to a canza min suna yanzun nan adai na yimin abu kamar bani da suna arika kirana da sunan babu." ban yi magana ba sai zare nonon da nayi abakin yaron ganin yayi bacci, na gyara na shinfiÉ—a shi, sai na yunkura ina kokarin mike wa, cikin hanzari ya janyo ni na faÉ—o jikin sa, sai ya rungume ni yashiga ai kamin da zafafan sakwannin sa, masu birkita min lissafi, yashi nuna min yan da yayi missing É—i na na wanaki uku. duk kanin mu numfashi muke sauke wa a hankali ya kawo bakin sa saitin kunne na cikin yin kasa da murya yace "Kyakkyawa ta wani suna aka bani? oya faÉ—a min naji." a hankali cikin yanayin da yagama saukar min da kasala nafurta "My." wani irin runguma yayi min kamar zai cusa ni cikin kijin sa yace "Wlh yayi kai amma gaskiya ni mai sana ne komai kin iya kamar yan da kika iya haifo min wannan kyakkyawan santalenen yaron nan haka kika iya zaÉ“ar min sunan da ya dace da ni, ina son ki HAMDAH ina yimi ki son da banayi wa kaina." bakin sa ya dadaÉ—a mayar wa cikin nawa, nan ma yashi sau ke min wata sabuwar kasalar, tuni idanunsa ya gama sauya wa sai fidda numfashi yake. gaba É—aya ya birkice yakuma birkita ni, joystick É—in sa ya damke da hannun sa da karfi a hankali cikin fizgar numfashi yace "Zafi yake min ki tai maka min." ido na waro nace "Ta ina ko ka mance akwai jini kuma akwai ciwo agurin." kai ya girgiza yace "Na sani bata nan ba." sai ya cusa hannunsa cikin wando yazaro sa, yana tsaye kem sai zillo yake. hannuna ya kamo duka biyu ya saka kansa yaÉ—an matse, fahimtar me yake nufi da sauri nace "Inna Wuro zata shigo fa." yace "Bazata shigo yanzu ba." a hankali na gyara na shiga kokarin taimaka masa ta hanyar sarrafa shi da hannu da kuma baki na, dan nasan yana buÆ™atar taimako na a wannan lokacin duba da yanda yake ta matse ido. sai da na tabbatar da nasama masa nutsuwa kana na zare bakina kan abar tasa, nayi amfani da toilet paper wajen kawar da madarar sa. sumbatar goshi na yayi tare da faÉ—in "Nagode sosai kyakkyawa ta." idanuna na lumshe tare da kuma buÉ—e wa... Ya juya yana faÉ—in "Bari naje nayi wanka." bayan sa nabi da kallo har ya fita, sai na sauke numfashi tare da mai da bayana na jingina da jikin gado a hankali na lumshe idanuna. fitar sa da kamar minti 30 Inna Wuro ta shigo, ta leko fuskar yaron tace "Bacci yake ne?." nace "Eh." kofin da ta shigo dashi rike a hannun ta ta mika min tana taÉ—in "Gashi kisha maganin da Malam yace a dafa miki ne." nace To tare da karÉ“a, nace "Inna Wuro kinji sunan da ya sa wa yaron nan wai Ahmad." Inna Wuro tayi dariya tace "Ai yanzu yake faÉ—a min a hanya ta tazuwa nan, nace to kaji Ahmad baban Ahmad, Allah ya raya shi da imani yaÉ—au ko halin uban sa da kakasan sa." nace "Wai fa haka za'a rika kiran sa nace a canza masa yace a'a taya za'ayi a rika kiran sa da sunan." tace "To shi haka yaga yafi tun da shi yace sai a rika kiran sa da hakan kawai." kai kawai na girgiza kana nashiga shan maganin.. Washegari da sassafe Hajiya Karima tazo lokacin ana shirin yiwa Ahmad karami wanka, a parlour'n sama ta zauna, sai da Inna Wuro tayi masa wanka ta shirya shi kafin ta mika wa Faty da ke zaune tana zaman jiran a gama masa wankan a bata shi. Inna Wuro tace ta kai wa kakar sa shi a parlour. sai a lokacin nima na mike na fita parlour'n, Faty tazo daf da ita zata mika mata É—an mukajiyo maganar Ahmad a sama. "Da kata Faty!." cak Faty ta tsaya batare da ta mika mata É—an ba, É—an razana Hajiya Karima tayi a É—an daburce ta É—ago kanta. ya karaso cikin parlour'n yayin da idanunsa ke kan hannun Hajiya Karima, Rasheedat na biye da shi..........! 29 Da sauri cikin dabara Hajiya Karima ta mai da hannun ta cikin mayafin ta. murmushi Ahmad yayi ya mika hannu ya karÉ“i Ahmad karami yana faÉ—in "Ke Faty haka ake rukon yaro a garin ku? ya zaki fito da shi a sanyin nan babu wani isasshen kaya a jikin sa, bani shi nan budurwar kauye kawai." Faty tace "Kai Yaya Ahmad ba ga kaya ajikin sa ba." yace "Ke yaushe kika san yan da ake rainon É—a haka zakije gidan ustaz É—in nan kina fidda masa É—a babu kaya a sanyi ko." dariya tayi tana rufe fuskarta. baki na buÉ—e nace "Wani Ustaz É—in?." yace "Ita ta sanshi ai." da sauri tayi waje tana faÉ—in "Ni babu ruwa na." ya dubi Hajiya Karima yana daÉ—a faÉ—aÉ—a murmushin sa yace "Hajiya so take tasa angon ki ya kamu da mura wannan kayan ai baiyi a fito da shi ba." baki Hajiya Karima ta washe cikin É—an kame-kame tace "Eh haka..haka ne." wani murmushin yakuma sake wa kana ya juya ya shige cikin bedroom É—ina. zuwa can yafoto da shi cikin wani katon towel ya karaso inda take ya mika mata shi yana faÉ—in "Hajiya ga angon naki." baki ta washe tace "A'a kaga Ahmad É—an Ahmad jika ga Tijjani sabil, kaman kai lokacin kana jariri." baki ya washe yana zama kan kujerar da ke fuskantar ta yace "Hajiya da gaske haka nake lokacin ina jariri anya nakai sa kyau lokacin kuwa?." tace "Sosai yan da ka ganshi haka kake kai da gashi har yanzu kyan naka na nan bai gushe ba." kallo na yayi tare da É—aga min gira. niko baki na taÉ“e a É“angaren Aunty Rasheedat ma haka a bin yake itama bakin ta taÉ“e sannan tace "Hajiya kice kun sha kallo lokacin can." fuska Hajiya Karima ta É—an suke tana yimata kallon kasa-kasa. itako Rasheedat wani murmushi ta sake tare da jijjiga kai. Ahmad kuwa idanunsa a kan É—an da kuma hannun Hajiya Karima. tana kokarin mike wa da sauri shima ya mike yana faÉ—in "Hajiya badai tafiya zakiyi ba?." dariyar yake tayi tace "Gidan wani biki nake son zuwa direba ma yana waje ya zaman jira na, dama nazo ne naga jikar nawa gashi nan sai baccin sa yake Allah ya raya mana shi muga girman sa." karÉ“ar É—an yayi a hannun ta yace "Amin amin gun gode Hajiya." yayi mata sallama ta fita. tana fita ya matso in da Rasheedat take ya zauna tare da jan towel É—in da ya naÉ—e yaron ciki yace "ÆŠau ke shi ban da towel É—in." ta É—ago shi da iya abin É—aukar sa da É—azu aka fito da shi ta rungume shi a jikin ta tana sumbatar goshin sa. shiko Ahmad mike wa yayi rike da towel É—in a hannunsa yanufi kasa.. numfashi Rasheedat ta sauke dan tasan komai akayi akwai wani abun. ta dubeni da murmushi ganin yaron ya farka yana mutsumutsu tace "HAMDAH bashi nono kin ga ya farka." nace "Allah Aunty Rasheedat yaron nan yafiye tsotso Allah ni bacci ma nake ji kuzau na da shi kawai ki bashi madara ya sha." na mike tsaye na nufi bedroom É—ina. dariya tayi tace "Madara kuma ah da sauran sa tukun kidai tai maka ki bashi É—in." ta biyo nita cigaba da faÉ—in "HAMDAH karÉ“e shi kibashi kin ga zai yi kuka." Inna Wuro da take cikin É—akin tana gyara, ta karÉ“e shi ta miko min shi... Rasheedat na fita daga É—akin lokacin Ahmad ya hauro, da fuakar tambaya ta dube sa, sai ya ruko hannun ta ya janyo ta cikin bedroom din da suke kusa da shi. suna shiga tace "Aboki me ke faruwa ne ina kakai towel É—in?." numfashi ya sauke yace "Nasa aje a yar da shi ne, tazo da wani irin guba mai amfani da fatar jiki yana saurin yiwa yara musamman jarirai illa acikin mintuna kalilan, shine a hannunta duk da yana cikin kwalba amma yana da hatsarin gaske, taso yin amfani da shi wajen sakawa yaron a jikin sa, bayan Æ´an mintina kuma zai shige cikin jikin sa daga nan kuma sheke nan, fatan jariri bashi da karfi koda kwalbar kaÉ—ai ya taÉ“a jikin sa za'a iya samin matsala, shiyasa na saka masa towel É—in nan ta in da koda kwalbar ya taÉ“a shi ma zai tsaya a iya jikin towel É—in ne." Ido Rasheedat ta waro cike da tsananin tsoro tace "Aboki ya kamata kayi wani abu fa, matar nan babu É—igon imani tare da ita, zata iya bin tawata hanyar tun da taga yanzu bukatar ta bai biya ba, nikam nafara jin tsoro." murmushi yayi yace "Babu abin da zata iya yi." tace "To amma dai zaka faÉ—a wa HAMDAH ko dan tasan me ake ciki tadaÉ—a sanya ido sosai, kada ranar da baka nan kuma tazo." yace "A'a baza'a faÉ—a mata ba idan aka sanar mata hankalin ta zai tashi dan ba ni da É—an kaÉ—ai take hari ba har da ita, idan taji kuma hankalin zai tashi za'a iya samin matsala." cikin kaÉ—uwa tace "Har da ita?." kai ya jinjina kana yace "Muje babu komai." Ana gobe suna da daddare Ahmad ya shigo, Inna Wuro na ganin sa ta fita, É—an madaidaicin akwatin da ya shigo da shi ya aje kan table, sai da ya sumbaci goshina sannan ya sumbaci Ahmad karami dake bacci. yaÉ—a go kana ya zuge zip É—ip É—in akwatin wasu kaya ne na alfarma a ciki, dogayen riguna ce irin na amare haÉ—e da jaka da takalmi da sarka da Æ´ankunne da abun hannu na gold, tsayuwa kwatan ta muku kalar tsaruwan kayan ma É“ata lokaci ne, ya haÉ—u yayi kyau ya tsaru iya tsaru wa. da sauri na mike na É—ago É—aya daga cikin rigunar na manna shi a jikina nace "Wannan fa kai gaskiya sunyi min kyau sosai." murmushi yayi yace "Yanzu naje na amso su a airport jiya nasa a siya yau aka saka a jirgi." murna yahani tsayuwa naji daga wata kasa yasa asiya, naÉ—ago sarkar da sai wal-wal yake yana É—auke ido nace "Kai gaskiya wlh duk sun yi kyau sosai fa." dariya yayi yace "Ashe nima na iya zaÉ“e kenan." nima dariyar nace "Gaskiya yayi kyau sosai ka iya zaÉ“e kam." wayar sa ya É—auka ya daddanna yace "Zo ki gani." gefen sa na zauna ina leko cikin wayar. hotunan wani katon hall ne wan da tsaruwan sa yakai ya kawo yace "Anan za'ayi toron bikin mu dana suna gobe da karfe sha É—aya na rana za'a fara za'a tashi karfe 11 na dare." da mamaki nace "Ina a gida za'ayi taron." yace "Ina ai ba iya taron suna ba ne kaÉ—ai har da taron bikin mu, yanzu haka ina da ba'ki waÉ—an da suka zo daga kasashe masu nisa sosai suna masaukin da a ka tanadar musu wasu kuma zasu iso cikin dare wasu gobe da safe." kai na jinjina jin da faske yake nace "Allah ya kaimu, Ukhtee ma ta kusa iso wa wata kila jirgin su ya sauko karfe 9." yace "To bari a sa direba ya shirya zuwa taro ta, ya kamata ya isa airport kafin saukowar su." kira ne yashigo wayar sa ya mike yana faÉ—in "Wani abokin Daddy na ne daga É—an Nigeria ne mazaunin Ingila, jirgin su ya iso kenan bari naje nasa a taro shi, bani number Ukhtee na baiwa direba ya tafi yanzu time zai yi." nace to. ina bashi yafita da sauri. da misalin karfe 9 kuwa jirgin su Ukhtee ya sauko, direba ya É—auko ta zuwa gida, har farfajiyar gida naje na taro ta, muka rungume juna muna ihun murna. ranar kusan kwana muka yi muna hira... Washegari tun sassafe Hajiya Rahama tazo da me makeup dan jiya mun yi waya da ita, bayan nayi wanka na zauna a ka shiga tsantsara min kwalliya, ana gamawa nasa Ukhtee ta zaÉ“o min É—aya saga cin kayan da jiya Ahmad ya kawo min, na saka na zauna me kwalliyar tashiga naÉ—e min É—ankwalin kayan a kai tana gama É—aurin, aka miko min takalli da É—an madaidaicin pos wan da suma acikin akwatin aka ciro su, nasaka takalmin narike pos É—in a hannu sai É—an karamin gyale wan da aka rataya min shi a hannu, karfe 11 da minti goma a ka gama yimin komai, kowa ya tsaya kallo na kamar basu taÉ“a ganina ba, sai faÉ—i suke Masha Allah. Aunty Nasiba da Faty da Ukhtee sai hotuna suke ta yimin. hannu na wacce tayi min makeup É—in ta ruko muka tako gaban mirror mirror'n tayi min nuni da shi tare da faÉ—in "Bismilla." ina sauke idanuna kan mirror sai da naÉ—an girgiza, sosai na kure kaina da kallo ta cikin mirror. sai nake gani kamar ba ni bace, "Masha Allah." nafaÉ—a a kasan raina, ni kai na nasan nayi kyau ba na wasa ba. kiran Ahmad ne ya shigo waya ta na É—aga yace "Ki fito gani a waje time yayi fa har yaÉ—an go mun bar mutane acan." nace to, nayi wa Ukhtee magana da larabci kan ta karÉ“i Ahmad karami dake nannun Hajiya Rahama wan da shima aka shirya sa cikin kayan alfarma wan da É—azu Aunty Rasheedat ta aiko dashi tace a sa masa. muka fito gaba É—ayan mu, tsayuwa nayi ina kallon kayan dake tare cikin parlour Inna Wuro da wasu ba'ki suna zaune suna kallon kayan, nan Inna Wuro take faÉ—a min dangin Ahmad ne suka kawo. nace mata zamu tafi gurin taron ne ko zata je, tace min a'a ita kam tana gida. wasu daga cikin mutanen cikin parlour'n suka mike suka ce suma zasu. a parlour'n kasa na iske mutane tam wasu ma ban san su ba. nan muka É—unguma mukayi waje. motoci ne ajere a tsakar gidan da suka kai guda goma, motar sakiya an bita da wani kalliyan furanni ta sama da gefe-gefen ta, kuma kaf cikin su rafi kowani mota kyau. da sauri wani soja dake tsaye jikin motar ya buÉ—e marfin gidan baya, can na hango Ahmad yana leko ni. a hankali na karaso jikin motar, da sauri sojan yayi baya ya daÉ—a buÉ—e marfin motar, a sannu na shiga nayi wa Ukhtee magana nace ta shi gaba. sojan ya mai da marfin ya rufe. kana ya buÉ—e mata itama ta shiga, acikin motar na tadda su Naseem sun sha wanka na alfarma kayan su iri É—aya Nasmah har da makeup a fuskar ta, sun yi kyau sosai. shima Ahmad É—in wani kaya ne a jikin sa na alfarma agogo da takalmin kafar sa sai sheki suke. ido Ahmad ya kura min babu ko kiftawa yabuÉ—e baki da hanci gaba É—aya yana kallo na. iska na hura masa a fuska nace "Ya dai?." firgigit yayi sai yapl damko hannuna yace "Kyakkyawa ta kin gan ki kuwa kin ga yan da kika daÉ—a kara kyau." murmushi nayi nace "To ai kai ma kayi kyau." baki su Naseem suka shiga washe wa suna faÉ—in "Mommy tayi kyau." nace "Kuma kun yi kyau." Ahmad suka gaisa da Ukhtee yana yi mata ya gajiyar hanya. jama'a kowa ya shishiga mota a ka ja motocin a jere aka É—au hanyar hall É—in. tun daga farkon shiga layin da zai sadaka da hall É—in jami'an tsaro ne ke tsaitsaye har bakin get É—in, baka jin komai sai tashin sautin kiÉ—a, a hankali aka wangale get É—in motoci suka kusa ciki, cikin katon farfajiyar gurin cike yake da motoci, a haka aka rika faka motoci layi-layi. sauran motocin da muka zo da su duk mutanen ciki suka fita suka nufi cikin hall É—in, muna zaune cikin motar har waÉ—an da suka zo daga bayan mu suka shige ciki. zuwa can Rasheedat ta fito daga cikin hall É—in, cikin shigar ta na burge wa irin shigar manyan mata matan manyan mutane. ta karaso jikin motar in da wasu sojoji guda huÉ—u suka mara mata baya, ta buÉ—e gefen da nake fuska É—auke da murmushi tace "Ku sauko ku ake jira." a hankali na zuro kafafu na waje na mike tsaye, É—aya daga cikin sojojin ya zaga da sauri ya buÉ—e gefen da Ahmad yake, shima ya fito, sannan a ka buÉ—e wa Ukhtee tafito rungume da Ahmad karami. Naseem da Nasmah ma suka fito. cikin harshen turanci Rasheedat tace wa Ukhtee ta bata É—an bayan sun gaisa tayi mata maraba da zuwa kasar mu... Naseem da Nasmah suna gaba ni da Ahmad muna biye da su, in da Rasheedat da Ukhtee ke bayan mu, Rasheedat nata gefen Ahmad Ukhtee kuma tana ta gefe na. haka Rasheedat ta tsara yan da zamu tafi a jere, takuma bawa Naseem da Nasmah wasu fulawa masu kyan gaske suka rike a hannun su. a hankali muka fata takawa a sannu har muka isa bakin kofar da zai sada mu da ai nahin cikin hall É—in. a sannu muka kusa ciki, wani irin wal-wal haka hasken camara ke haska mu, a take aka saiya kiÉ—a aka saki wani zazzakar waka mai kwankwasa zuciyar masoya, ga mamaki na sai naji sunan mu ake ambata cikin wakar, gaba É—aya cikin hall É—in yaÉ—au ki tafi raf-raf-raf, yayin da MC yashiga zuba kirari. "Gafa taurarin sun danno farin wata sha kallo an gai da ango da amarya." sai ya shiga bin wakar da ke tashin yana faÉ—in "Ga HAMDAH sarauniya mata ga Ahmad sabil uwa ga Ahmad kaga mai farar aniya." a hankali nake É—aga kafata da naji tana yi min nauyi dan jama'ar da na gani cike a gun. yayin da aka cigaba da haska mu da camara. har muka isa mazaunin da aka tanadar mana, kuje rune guda huÉ—u a jere sai wasu biyu Æ´an madaidai ta a ta kasa da namu wato step É—in dake kasa da mu. a biyun tsakiya muka zauna ni da Ahmad Rasheedat ta zauna a gefen sa in da Ukhtee kuma ta zauna a gefe na, Naseem da Nasmah kuma a biyun da ke kasan mu. muna zama kuwa camara suka cigaba da haska mu, Æ´an jaridu ma aikatan gidajen TV ne ta ko ta ina a gurin sai É—auka suke. nan da nan akafara gudanar da biki, yayin sa Æ´an wasan hausa da mawaka kowa ya fito yana nuna bajin tar sa. taro yayi taro anyi É“arin kuÉ—i, ma'aikatan hotel da akayi odar su hotel daban-daban da suka girka kalolin abinci kala-kala. sai zubawa ake ana kaiwa tebur-tebur. MC yace ana bukatar ango da amar ya su fito, Rasheedat ta É—an karkato in da yake tayi masa maga, sai ya riko hannuna ya mike kana ya mikar da ni, a hankali muka sauka muka shigo cikin filin. wani kiÉ—an aka kuma sakewa shima da sunan mu cikin wakar. yana rike da hannuna dukan mu muna tsaye, kai na na sunkuye, yaÉ—an sunkuyo da kansa dai-dai fuskata yace "Bazaki yi rawa ba." kafaÉ—a na make cike da jin kunya nace "Ban iya ba." yanayin yan da muke maganar da shi hakan yabada wani irin kala, ai ko hall É—in ya kaure da ihu da tafe. cike da jin kunya na kife kaina jikin kafaÉ—ar sa. hannu ya zura cikin aljuhu yaciro É—aurin kuÉ—i Æ´an 1-1k sababbi katakar yashiga lika min, yana murmushi ban É—ago ba kai na najikin kafaÉ—ar sa, sai da naji maganar Rasheedat daf da ni tana faÉ—in, "Ba zakuyi rawa ba." sai na É—ago tare da girgiza mata kai ina murmushi. liki tashiga yi mana tarika ciro kuÉ—i cikin jakarta tana wasa mana, ta dage tarika tika rawa. nan manya manyan mutanen dasuka taho daga kasashe daban-daban suka rika shigowa filin suna lika mana kuÉ—i, wasu kuÉ—in kasar mu wasu kuma na kasashen da suke... kai tsaye ake nuna shagalin bikin dan daga can jikin bangon hall É—in katuwar majiki ne ke haska duk abin da ke faruwa.. biki yayi biki naira tayi kuka agurin.... A can cikin garin Bauchi Masa'ud ne kwance cikin É—akin sa da waya rike a hannunsa, yana kalle-kalle a yana gizo, ido ya kurawa wani bikin da yaga ake gudanar wa,gani har ya shari kusan minti 5 bai ga shigowar ango da amarya ba sai ya wuce. yana yin gaba kuwa yakuma cin karo da wannan bikin da ake hasko sa kai tsaye. da mamaki yakurawa amaryar ido tare da maimaita sunan da yaji MC yana kira "HAMDAH!." yafurta da karfi, yayin da hannunsa yashiga É“ari idanunsa a kan fuskarta, duk da ta kara girma da kuma kwalliyar dake fuskarta tabbas bazai taÉ“a iya mance fuskar nan ba. da sauri ya mike yayi waje har yana cin karo. tun daga bakin kofar side É—in Mamie yashiga kwaÉ—a mata kira "Mamie Mamie Mamie." kasan cewar yau weekend ne su Aunty Rafee'at da Aunty Jaleeta sun zo gida dukan su da Æ´aÆ´an su, Na'ima ma tazo da nata É—an, duk suna hallare a sashin Mamie har da Ummi. da sauri Mamie ta É—ago jin irin kiran da yake kwaza mata sai kuma gashi ya faÉ—o cikin parlour'n kamar an jefo sa, ko gaban sa baya gani. tace "Kai Masa'ud wani irin hauka ne haka, bazaka shigo ba tun daga waje kake lafta min kira irin haka kamar wani sabon makaho." da sauri ya karaso in da take kamar zai faÉ—i a kan ta hannunsa na É“ari yace "Mamie kigani Mamie HAMDAH HAMDAH ce." sai kuma ya sake wa Mamie wayar da sauri ya juya ya fizge rimut É—in da ke hannun Nusaiba ya daddan na sai gashi ya kamo É—aya daga cikin tashoshin da ake haska bikin kai tsaye..............! Mommyn Twins ce 8/19/22, 10:58 - Ummi Tandama😇: 30 Masa'ud da gaba ki É—aya ya jikin sa ya kama suma kamar zai tashi sama yace "Mamie kun ganta wlh itace HAMDAH ce ga ta nan itace wannan." yakai hannu yana taÉ“a jikin TV dai-dai fuskar ta. gaba É—aya cikin parlour'n suka mai da hankalin su kan TV. Aunty Rafee'at ta mike da sauri tazo jikin TV tana karewa wanda Masa'ud ke nunawa kallo, da karfi ta furta "Wlh ita ce wlh HAMDAH ce wannan, masa musu su gani Masa'ud masa su ganta." tayi maganar tana ture shi gefe. Ummi da tayi mutuwar zaune tana kallon abin mamaki, sai ga hawayen farin ciki yana fitowa daga idon ta. yayin da bakin ta ke ta furta kalmar "Alhamdulillah³." Mamie kuwa abun kamar a mafarki take ganin sa yayin da zuciyar ta ke ta son tunano mata abubuwan da suka faru abaya, yayin da wani abu ya taso yake ta son danni hakan. kokawa tashiga yi sakanin zuciyar da wannan abun da ke ta faman son danne hakan, lallai ba shakka wannan HAMDAH ce, duk da girma da cika da sauyin da ke tattare da ita, koda shekaru É—ari tayi basa tare bazasu kasa gane jinin su ba. wasu zafafan kwalla ne masu É—umi suka zubo mata, takasa iya furta komai kamar yadda ta kasa janye idanunta daga kan TV. hannunta na rawa ta shiga nuna TV da yatsa yayin da bakin ta yakasa iya furta komai, sai zafafan hawayen da suka cigaba da wanke mata fuska. Da gudu Aunty Jaleela taje ta rungume Aunty Rafee'at tana faÉ—in "Wlh ita ce HAMDAH ce Aunty Rafee'at da gaske ita ce." Nusaiba da Fauzan ma suka mike suka rungume suna faÉ—in "Aunty HAMDAH ce wlh ita ce." parlour'n ya kaure da hayaniya da ihun murnar da su Aunty Rafee'at suke.. A É“angaren Na'ima kuwa tun san da ta sanya idanunta kan HAMDAH dake cikin TV, tayi wani irin daskarewa a zaune a gurin, wani irin bugawa kirjin ta yayi da mugun karfi har sai da takai hannu ta dafe kirjin nata. su Abbu da suke zaune cikin parlour'n da suke zama shi da Abba, jin hayaniyar dake fita daga cikin side É—in Mamie yayi yawa sai suka mike da sauri suka fito. dai-dai lokacin motar SALEEM yashigo gidan, daga cikin mota ya hangi yan da su Abbu suke sauri suka nufi side É—in Mamie. cikin hanzari ya faka motar yafito yarufa musu baya. a kusan tare suka shiga parlour'n Mamie Abbu ya buÉ—i baki da zumbar tambayar abin da kefaru idanunsa ya sauka kan TV dai-dai lokacin da aka hasko katon hoton HAMDAH wan da ya maimaye fuskar TV gaba É—aya, inda É—an jarida yake faÉ—in "HAMDAH kenan shahararriyar Æ´ar kasuwan nan wacce aka fi sani da *HAM'NAS CO PETROLEUM NIGERIA LIMITED* ayau ne ake gudanar da shagalin bikin su da kuma murnar samun karuwan É—a da sukayi, ita da mijinta shahararren attajin nan shahararren É—an kasuwan nan wacce duniya ta sanshi wato *AHMAD TIJJANI SABIL* ." sai a ka É—auke hoton ta kana aka kuma sakin wani katon hoto, tana tsaye rike da jariri Ahmad na tsaye a gefen ta ta dama yaÉ—an leko fuskar ta suna yi wa juna murmushi, in da Rasheedat ke tsaye gefen ta na hagu, Naseem da Nasmah suna tsaye a gaban su suna dariya, É—an jaridar yaci gaba da faÉ—in "Kai tsaye ake gudanar da shagalin bikin, gamu nan a filin taron, biki yayi biki jigajigan shararrun Æ´an kasun nan kuma ma'aurata Ahmad Tijjani Sabil da amaryar sa HAMDAH wacce akafi sani da *HAM'NAS* Co petroleum Nigeria limited,suna cike da murna da farin cikin kuma samin karuwa da farin cikin karuwan family'n su, muna nan zamu cigaba da kawo muku yan da bikin take kasan cewa a filin taron kai tsaye kucigaba da biyo mu." shagalin bikin aka cigaba da nunawa... Kamar a mafarki kamar abun almara haka dukkanin su suke kallon. yanayin da Mamie ta shiga shi Abbu ya shiga, sai nuna TV yake da yatsa, Abba kam baya yayi ya jingina da jikin garu yayin da idanunsa shima ke kan TV. a É“angaren SALEEM kuwa wani irin wawan burki yaja yatsaya cak daga bakin kofa, yayin da zuciyar sa tayi wani irin tsalle tamkar zata faso kirjin sa ta fito, wani irin rumtse idanunsa yayi da mugun karfi yakuma ware sa a kan TV, dai-dai lokacin da Ahmad ya rungumo ta ita da baby'n su suna dariya, yayin da wani bature yake yi musu liki. da karfi ya kai hannunsa ya dafe kahon zuciyar sa,da yake wani irin tafarfasa, wani tari ne ya suÉ“uce masa yashiga yin sa babu ko kakkautawa yana mai cigaba da damke kirjin sa, baya yashiga yi hannunsa na dafe a kirjin sa. Masa'ud ne yalura da halin da yake ciki da sauri ya isa in da yake, ya yana faÉ—in "Ya SALEEM sannu ka shake ne bari na kawo maka ruwa." hannu ya É—aga masa kana yayi waje dafe da kirjin sa yana mai cigaba da tarin... zumbur Na'ima da zufa yashiga keto mata ta mike tsaye ta tsaÉ“e É—an ta tayi waje da sauri, mai adaidaita ta tsare yakai ta gida, tana shiga gida hankali tashe takira kawar ta Raliya a waya tana É—agawa tace "Raliya kina ina." jin yan da tayi maganar hankali tashe yasa Raliya faÉ—in "Aminiya me ya faru? ina gida yanzu dai nake shirin fita." tace "Kizo gida yanzu-yanzu akwai matsala." Raliya tace "Wacce irin matsala kin tsinkar min da gaba." cikin tsananin tashin hankalin da take ciki tace "Ashe yarinyar nan bata mutu ba tana nan a raye, ashe ita ce mai kamfanin *HAM'NAS* mai *HAM'NAS* Co Petroleum Nigeria Limited." Raliya tace "Wai wa kike magana ne kam ban gane ba." tace "HAMDAH HAMDAH nake faÉ—a." da karfi Raliya tace "Wacce HAMDAH ke bari gani nan zuwa." tana kashe wayar ta zari makullin mota tayi waje, tarika kai wa da kawowa a parking space har Raliya ta iso. Raliya tace "Wai me kike faÉ—a min ne kina nufin kice min HAMDAH bata mutu ba tana raye kuma anan kusa?." da sauri Na'ima tashiga mota tana faÉ—in "Shiga shiga zakiji komai a hanya kada mu É“ata lokaci." Raliya na shiga ta figi motar da mugun gudu suna fita a gidan Na'ima ta dubi Raliya hankali a mugun tashe tace "Aminiya HAMDAH na da rai ko kin san ita ce me kamfanin *HAM'NAS* sai gata É—azu ana nuna ta a TV ita da wannan mai kuÉ—in Ahmad Tijjani Sabil amatsayin miji da mata, Raliya ina cikin muguwar tashin hankali gurin boka zamu je yanzun nan, shi da yace baza a sake jin É—uriyar ta ba kwasam sai na ganta cikin daula, dole na sake sabon shiri ya daÉ—a jefa ta can da nisa taya ne ma ta kasan ce haka ina wlh da sake wai HAMDAH ce tazamo mai kuÉ—i kuma wai har ta auri hamshakin attajiri, wani bokan ne yabata sa a haka." kirji Raliya ta buga tace "Wai da gaske HAMDAH ce mai kamfanin *HAM'NAS* amma taya akayi haka? kai amma ni ina da kokon to kan lamarin." Na'ima tace "Ga abu a fili a TV naganta da idanuna ba faÉ—a min akayi ba mu gurin boka bamuyi haka da shi ba maza-maza yakashe ta kawai idan ba mutuwa tayi ba bazan taÉ“a samin sukuni ba." gudu Na'ima take shararawa har suka iso dajin da bokan yake, a gindin bishiyar da suke faka motar su a duk san da suka zo gurin bokan a nan suka faka motar suka fito. da sauri nufi in da bukkan bokan yake, tun kan su haura kan tudun da zai sada su da bukkan suka rika jiyo gurnani da wani irin kala mai firgitar wa,cike da fargaba Raliya ta dubi Na'ima tace "Ko kinji abin da nake ji?." cikin bushewar zuciya Na'ima tace "Naji yanzu haka wani gagarumin ai ki yake muje a shigar da namu gaba É—aya ayi akashe ta na huta." suna haurawa saman tudun babu shiri suka ja wani wawan burki, gaba É—ayan su jikin su ya É—au É“ari. bakon suka hango kwarkwasa sun maye jikin sa tun daga saman sa har kasa ko fuskar sa ba'a iya ganin, sun cike ko ina a jikin sa, kunne ido baki hanci ta ko ta ina sun baibaye sun rufu a jikin yam-yam. shiko sai wani irin kara da gurnani yake, sai ya yanki jiki ya faÉ—i akasa ya goga fuskar sa a kan duwatsun da suke gurin yayi ta goga wa jini yana fita, yakuma mike wa yakuma faÉ—uwa kamar wan da ake É—aga shi ana buga shi da fuska, kwarkwasar nan kuma suna nan a jikin sa. da mugun gudu suka juya ganin wasu kwarkwasa suna gangaro wa in da suke, nan take bokan nan yakuma yin sama kamar wan da aka É—aga shi sai gashi cikin wutar da yake hurawa domin yin wani asirin sa ko shan É—umi. yayi ta birgima yana bige-bige da kara haÉ—a da gurnani mai firgitar wa cikin wutar. Raliya da Na'ima har suna rige-rigen shiga motar har gindin motar kwarkwasar na suka biyo su Na'ima ta ja motar a guje suna waigen bayan su da duba kasan kafar su ko kwarkwasan sun biyo su.. sai da sukayi nisa sosai kafin Na'ima ta dubi Raliya tana haki tace "Raliya boka ya mutu yanzu meye mafita?." Raliya tace "Gurin wani bokan zamu je ai basu kare ba." daga nan suka nufi gurin wani bokan da Raliya ta faÉ—a mata ita ma wata kawar tace ta nuna masa gurin sa. suna zuwa bayan sun gama zayyane abun da ya kawo su, bokan yace ta ajiye miliyan 10 wan da za'a fara ai ki da shi, dan ai kin nata babba ne. babu wani dogon nazari ko tunani ta ajiye masa check É—in miliyan 10. yace suje nan da kwanaki biyu su dawo... A É“angaren su Ummi kuwa kowa ya tsurawa TV ido in da ake kan cigaba da gudanar da biki, yayin da su Ummi Mamie Aunty Rafee'at Aunty Jaleela Ya Masa'ud Fauzan Nusai ba, duk kanin su hawayen farin ciki ne ke zuba kan fuskokin su. Abba da Abbu kuwa ido suka zubawa TV kawai, har kuma lokacin suna tsaye da Æ™afafun su, duk kanin su kuma sun kasa iya furta komai sai zuciyoyin su dake ta ambaton sunan Allah dayi masa godiya. a hankali suka rika jin zuciyoyin su tana washewa tamkar ana É—aga musu wani nannauyar dutse data danne musu zuciya. Abba Abbu Mamie a tare suka dafe kirjin su da suka ji kamar an fincike wannan abu mai nauyi an cire sa gaba É—aya, a tare suka sauke nannauyar numfashi... a É“angaren SALEEM da tun fitar sa daga parlour'n É—akin Masa'ud ya shiga ya kwanta kan gadon sa, dafe da kirjin sa har kuma lokacin yana dafe da kirjin nasa, wacce take yi masa wani irin mugun zafi, a take shima yaji kamar an fige masa wani abu mai nauyi cikin zuciyarsa, sai dai zafi da zugin da zuciyar tasa take masa... Acan cikin parlour'n kuwa Mamie ne tayi wani irin mike wa tare da furta "Wlh HAMDAH ce tabbas ita ce, Alhaji baka ganta ba?." tayi maganar tana duban Abbu. Abbu yashiga gyaÉ—a kai yana nuna TV da yatsa tare da faÉ—in "Tabbas ba shakka ita ce." wani hawayen farin ciki ne yakuma zubowa kan fuskar Ummi, ganin yan da sukayi firgigit tamkar waÉ—an da suka farka daga bacci, tasan dole watarana gaskiya zatayi halin ta. Abba kuwa cikin matukar nadama yake kallon É—iyar tasa daga cikin TV..... Abuja Har wajen magriba ana ta kan gudanar da shagalin bikin, salla ce kaÉ—ai take É—aga wasu agun. da misalin karfe 11 na dare aka rufe taron bayan an cike waÉ—an da suka zo bikin da kayan da Ahmad yasa a tanada domin duk wan da ya ziyarci bikin, duk wan da yazo bikin idan mamace turamen manyan zani guda biyu da kuÉ—in É—iki naira dubu goma acikin jaka mai É—auke da katon hoton Ahmad karami a jiki. idan kuma na miji ne tsadadden shadda ne shima guda biyu haÉ—e da kuÉ—in É—in kin sa a cikin jakar. a gajiye muka fito daga cikin hall É—in mota ta kwashe mu. ga mamaki na sai na ganmu a airport, da fuskar mamaki na dubi Ahmad nace "Rakiya muka zo ne?." da murmushi kan fuskarsa sa yace "Mu aka zo raka mu." nace "Ina?." nayi maganar ina waro ido. kuma tuna yaja kana yace "Lagos zamu, gobe za'ayi bikin buÉ—e Company ki na can, wan da É—ana ya hanaki samun sukunin buÉ—e shi." baki na buÉ—e zanyi magana sai aka buÉ—e marfin motar,gefen sa da fege na, sai nayi shiru na fito kawai. direct cikin jirge muka shige anan na tadda wasu daga cikin mutanen da suka halar ci bikin mu waÉ—an da suka zo daga wasu Æ™asashe har da wasu É—aiÉ—ai ku Æ´an nan kasar mu, a can kujerar gaba na hango Bappa yana zaune, acikin jirgin nake faÉ—a wa Ukhtee in da zamu je, na tausaya mata ganin yana yin ta na san tafaji sosai. a jere suka zauna da Aunty Rasheedat da Naseem da Nasmah, in da muka zauna ni da Ahmad a kujerar bayan su, yana rungume da Ahmad karami... muna isa motoci suka kwashe mu suka kai mu masauki, ni da Ukhtee É—akin mu É—aya Naseem da Nasmah kam ma ban ga idanunsu ba. a gaye muka shiga rage kayan kijin mu, ganin Ahmad karami ya nata mita nasan cewa wan ka yake bukata, na tuÉ“e sa nayi nashiga dashi bayi nayi masa wanka cikin bathtub dan dole sai dai nan É—in tun da ba bu wabon da zan masa a ciki, na naÉ—o sa a towel É—in sa na sauya masa wani kaya, dan gani kawai nayi an biyo mu da akwatin mu. sai da yayi bacci kafin na shimfida shi, lokacin Ukhtee tafito daga wanka, nima na shiga nayi wan ka, yau kam babu wani hira muna kwanciya dukan mu sai bacci.. washegari ban farka ba sai wajen karfe 9. ko da na farka na tadda Ukhtee har tayi wanka, ina dire a gadon Ahmad na buÉ—e ido, sai da na fara yi masa wanka kafin nima nayi. kayan breakfast É—in da aka shigo da shi tun ina bacci, bayan na shirya na zauna muka yi breakfast É—in, sai tan nan naje na É—au wayata da na kashe ta tun jiya isowar mu na kunna. ai ko ina kunnawa sai ga kiran Ahmad ya shigo, yace "Kyakkyawa ta an tashi lafiya ya gajiyan jiya." nace "Gajiya ya washe." yace "Alhmdllh Nagode wa Allah, ina Ahmad ya tashi kuwa ga su Naseem har yanzu basu farka ba." nace "Shikam ina tashi shima ya farka gashi nan yana ta rarraba idanu." dariya yayi yace "Sa masa wayar kusa da shi naji numfashin sa." wayar na kawo kusa da shi nace "Daddy na magana." murmushi yayi mai sauti yace "Shafa min kansa." nace To. yace "Anjima karfe 12 za'a tafi gurin nan, karfe 2 za'a gama yau zamu koma gida." nace "To Allah ya kaimu." yace su Naseem su tashi bari ya yi musu wanka zasu shigo nace to... Da misalin karfe 12 da kwata gaba É—ayan mu muka hallara a farfajiyar hotel É—in. nan motoshi suka rika kwasan mutane suna tafiya da su. kamar yan da muka tafi wancan filin taron jiya motar mu É—aya da shi yau ma haka, tun daga wajen kamfanin har cikin sa an zagaye shi da adon fulawa, a katafare filin da ke cikin kamfanin aka gudanar da taron, wan da mai girma Gwamnan Lagos shine babban bako a gurin taron da sauran mukarraban sa. an guda nar da taron cikin lumana da kwanciyar hankali in da ake nuna taron kai tsaye a kafafen sadar wa. anan gurin aka tantance ma'aikatan da suka nimi yin ai ki a kamfanin, aka kara akan wan da dama can aka tantace su kwararru masana ai kin... karfe 2:30Pm aka watse a taron kowa ya kama gaban sa, a ranar wasu suka koma kasashen da suka fito wasu kuma sai zuwa gobe. da misalin karfe uku jirgin mu ta É—aga zuwa Abuja. muna isa yau washegari Ukhtee tace zata koma, Ahmad yayi mata cuku-cukun komawa sai dai ba'a sami jirgin da zai tafi Saudi kai tsaye ba dole na dubai daga can sai ta shiga jirgin Saudi. har airport muka yi mata rakiya Ahmad na ta yi mata godiya, bayan cike ta da yayi da goma na arziki. lokacin da ake sanar wa kan fasinjoji su shigo cikin jirgi sai muka rungume juna muka fashe da kuka, da kyar Ahmad ya É“anÉ“are ni a jikin ta jin ana ta cigaba da sanar wan, ta wuce cikin jirgi muna É—agawa juna hannu... a mota yayi ta lallaÉ“e na har sai da yaga nayi dariya, ya dube ni fuska É—au ke da sihirtaccen murmushi mai bayyana zallar so da kauna yace "Ina son ki kyakkyawa ta." idanuna na lumshe kana a hankali na kwanto da kai na jikin kafaÉ—ar sa a hankali cikin yin kasa da murya nace "Nima ina son ka My." wani irin wawan burji ya ja, da sauri na buÉ—a idanuna na É—ago kaina da sauri cikin hanzar na dafe gefen kujerar moton jin yan da nayi gaba kamar zan garo da gaban motar. a gefen titi yayi parking, ya wani irin jan yo ni ya rungume tamkar zai cusa ni cikin jikin sa, yace "Nagode kyakkyawa ta Nagode da jin fitar wannan kalma daga bakin ki, ako da yaushe zaman jiran sa nake naji yafito daga bakin ki, ina son ki! ina son ki!! ina son ki!!!, ako da yaushe kamar daÉ—a kara min son ki ake." sai ya shiga sumbatar fuskata ta ta ta ina yarika manna masa kiss, ya ruÉ—e yagama zauce wa, sai kokarin daÉ—a nuna min yanda yake so na da kuma kauna ta yake. sai da na janye jikina da karfi nace Ahmad na gida zai iya yiwa Inna Wuro kuka. kafin ya ja motar muka bar gurin, yana tukin sai ya juyo ya sumbaci kuma tu na, aha muka isa gida. ranar bai matsa ko nan da can ba a yana like da ni, karshe Inna Wuro fita tayi ta bar mana side É—in gaba É—aya sai dare ta dawo.... Bauchi Ranar da aka gudanar da toron buÉ—e Company HAMDAH duk ka family'n su suna gindin TV, Aunty Rafee'at da Aunty Jaleela suna daga gida jen su suna waya a gida, cike da murna suna tambayar suma suna kan kallo ko. Ummi farin cikin ta har ya gaza É“uya duk tarin kawai cin ta. washegari da sassafe Ummi ta tashi da shiri, Abba ya shigo ya same ta tana ta shiri, da É—an mamaki ya dube ta yace "Shirin me kike ta yi haka?." tace "Gurin É—iya ta HAMDAH zani." ta faÉ—a a takai ce ta cigaba da shirin ta. Abba yaÉ—an yi gyaran murya kana yace "Yan zu muka gama magana da Yaya Idris ya kama ta ki bari mu shir ya tafiyar duka." da sauri Ummi ta É—ago ta dobe shi tace "Babu abun da zai hanani tafiya yau sai ikon Allah, idan kana tunanin cewa ma zaka kuma dakatar da ni ne, kamar lokacin da kayi ahakan a lokacin da take bukatar taimako da mafaka, na amin ta nayi maka biyayya to ka sani a yanzu bazan taÉ“a hanuwa ba, zan fita naje na nimo Æ´ata tun da har Allah ya nuna min tana nan da ranta, sai dai daga nan kakuma cewa kada na dawo maka gida, ko ban same ta ba na tabbata banyi asara ba." shiru Abba yayi yana kallon ta yayin da jikin sa gaba É—aya yayi sanyi, tabbas yasan Ummi mata ce mai hakuri da kawai ci, duk da shi ya kori HAMDAH da kansa ko dai-dai da rana É—aya bata taÉ“a nuna masa É“acin rai ba, kuma bata gushe kan biyaytar da take masa ba. yana tsaye tagama shirin ta ta É—au mayafin ta, taÉ—au jakar ta tayi waje. ya biyo yana faÉ—in "To ki tsaya direba ya kai ki." bata ko saurare shi ba. a sakar gida suka haÉ—u da Abbu ya tambaya ina zata, Abba ya faÉ—a masa, Abbu ya jinjina kai cike da yabawa da hakuri da kawai ci irin na Ummi yacewa Abba kada ya dakatar da ita da tafiyar, tafiyar nata shine zai samar mata da mutuwar data rasa shekarun baya da suka wuce tun barin HAMDAH gida, wan da ta rika dauriya da juriyar iya danne shi ta barwa ranta... Ummi na fita a dai-dai ta ta tsara ya kaita tasha daga nan ta shiga motar Abuja, idan bata man ce ba anan taga taron bikin farko da su HAMDAH sukayi, kuma taji Æ´an jaridun suna faÉ—in daga Abuja, taÉ—au haryan Abuja da tunanin idan ta neme ta bata same ta ba zata wuce Lagos in da taga an gudanar da taron buÉ—e kamfanin ta.........! 8/19/22, 10:58 - Ummi Tandama😇: 31 Koda Ummi suka iso Abuja ta sauka a tasha, tunanin ta in da zata fara ta shiga yi. mene ne abin yi tayi tambaya a babban gari irin wannan tana ganin kamar babu mafita a yin hakan, to amma ai HAMDAH ta sanu a yanzu wata kila baza ta sha wuya wajen samo ta ba. a da ire-iren irin waÉ—an nan tunanin ta tsare mai abun hawa, ko da mai taxe ya tsaya ya loko ta yana faÉ—in "Hajiya ina zuwa?." tace "Malam ko kasan gidan wata da ake cewa HAMDAH?." É—an shiru yayi alamun tunani kana yace "Gaskiya ban sani ba wace unguwar take?." tace "Ban san unguwar da take ba." yace "To in banda abin ki Hajiya zaki tsari mai abin hawa baki san in da zaki ba, a gari irin wannan zaki tambayi wata batare da sanin adireshin ta ba ai ba lallai ki iya samin ta ba ko a kauye ba'a haka bare a birnin tarayya." yaja taxes É—in sa yayi gaba. Ummi tace "In sha Allah zan same ta ko batare da adireshi ba." wani ta kuma tsare wa shima irin tambayar da tayiwa wancan shi tayi masa,kusan irin amsar da wancan ya bata irin shi shima wannan ya bata. ta tsari masu taxe da suka gai kusan guda goma duk kusan amsa iri É—aya suke bata idan tayi musu tambaya kan sun san gida wata da ake cewa HAMDAH... har yamma tana tsaye a bakin titi, wani mai taxe É—on taxe yazo zai wuce da ido kawai ta bishi dan har ta gaji da tsare masu abun hawa, ta fara tunani ta sami masauki ta huta dan ma Allah ya taimake ta tayi salla cikin tashan lokacin da suka sauka. har ya É—an gota ta sai ya dawo da baya yace "Ina zuwa Hajiya?. a É—an gajiye ta dube shi tace "Masauki mafi kusa da nan." yace "Hotel kenan?." tace "Eh." yace "To shigo muje." taÉ—au jakar ta tashige cikin motar da bismilla. har sun fara tafiya sai me taxe É—in ya É—an waigo kana ya mai da idanunsa ga titi yace "Babban hotel kike so a kai ki ko me É—an dama-dama?." tace "Me É—an saukin kuÉ—i dai wanda bazan kashe yafi dubu hamsin ba." kai ya jinjina kana suka cigaba da tafi, sun iso daf da hotel É—in me taxe yace "Yau wa gamu mun iso bari na karasa da ke can basai kin tsallaka ba sai ki shiga." tace to. baki ya washe "Amma Hajiya a garin nan fa komi dare ana samin mota duk garin da kike son zuwa zaki sami mota, ai da zai fi miki akan ki kashe kuÉ—i mai yawa gara ki shiga mota ki wuce gaba É—aya, ko da shike manya basu fiye son zaman mota da yawa ba wai shima wahala ce agurin su, kai talaka kam gara ka wuce É—in ka adana kuÉ—in da zaka nimi masauki kayi wata bukatar da shi." yakara sa maganar yana cigaba da washe baki. Ummi tace "Allah ya rufa mana asiri duniya da kiyama, amma ba wani gari zanje ba iya ka ta nan garin idan ban dace ba kuma sai na wuce Lagos, ni gidan wata nake nima tun É—azu na iso garin nan gashi har yamma tayi, ina ta tambaya ban dace ba." yace "Tambayar gidan wata a cikin garin nan, gaskiya zai yi wuyar samu in ba wai kasan adireshin gidan bane, to ke baki da lambar ta ne ki kirata tayi miki kwatance?." Ummi tace "Bani da lambar ta." yace "To gaskiya zaki sha wuya ne kawai wajen neman ta, manya ne waÉ—an da aka sansu akasar sune idan kashigo niman su cikin garinnan bazaka sha wuya wajen samun su ba, tun da sun sanu yawanci zakiga an san su, gaskiya zaifi ki koma gida ko kuma ki kira aturo miki lambar ta sai ki neme ta, amma ya sunan ta ko sunan take kusa da su wata kila manya ne tanan zaki iya dace wa?." tace "HAMDAH sunan ta." yace "Wai to Allah yasa ki dace." tace "Amin ngd." dai-dai nan yagyara fakin ta sauka ta biya sa kuÉ—in sa, taÉ—au jakar ta ta gangara hanyar da zai sada ta da cikin hotel É—in. har ta kai bakin get É—in hotel É—in taji ana faÉ—in "Hajiya Hajiya Hajiya." ta juyo dan gani ko da ita ake sai taga mai taxe É—in nan ne yayi ribas ya dawo da baya, kanta ta nuna alamun ita yace Eh. sai ta juyo ta nufi in da yake. kansa ya leko ta window motar yace "Hajiya kika ce meye sunan wan da kika zo neman ta?." tace "HAMDAH." yace "Babu wani inkiyar ta HAMDAH É—in ne kaÉ—ai?." shiru Ummi ta É—an yi tana son tuno sunan da taji an kira ta da shi a TV da kuma wan da ta taÉ“a gani a wani gidan mai. mutumin yace "Dama akwai wata ce me irin sunan nan sai dai tana da inkiya, mutane da dama basu san ta da ai nahin sunan taba sai inkiyar nata,sau É—aya nataÉ“a jin ainihin sunan nata shine nake tuna nin ko ita É—in ce." Ummi tace "Tabbas akwai sunan da ake kiran ta da shi amma naman ce." yace "To wata kila ba ita bace ni wanda na sani idan kuma ban mance ba HAMDAH baji an faÉ—a amma sunan da aka fi sanin ta dashi shine wan da take amfani da shi kan kamfanoni da gidajen mai asibitoti da sauran su, shine *HAM'NAS* ita kuma matar Ahmad Tijjani Sabil ne." da sauri Ummi tace "Kwarai kuwa tabbas ita ce so nake na tuna "*HAM'NAS* É—in na mance, dan Allah bawan Allah kai ni gidan nata." yace "To a gaskiya dai ni ban san gidan ta ba gidan Ahmad Sabil É—in kaÉ—ai na sani kuma ance gidan ta da ban ne, sannan kuma gidan sa a gaskiya akwai matakan tsaro ko na kaiki ma ba lallai bane a barki kishiga in ba wai an san da zuwan ki bane." É—an shiru yayi sai kuma yace "Amma dai shigo mu je tun da kin ce ita ce samun gidan ta bazai bada wuya ba sai muyi tambaya." godiya Ummi tashiga yi masa da addu'ar samun nasara a rayuwar sa. Tun daga gurin suka fara tambaya har suka sami wan da yayi musu kwatance har unguwar da take da kuma lambar gidan. suna isa dai-dai gida mai lambar da aka faÉ—a musu ya tsaya yace da ita sun iso, ta sauka tayi ta masa godiya kana ta baki 5k, ya karÉ“a shima yana yi mata godiya, kana yaja motar sa yayi gaba. ido ta zubawa katon gidan wan da tsaruwan sa ya kai ya kawo a ranta take faÉ—in. anya kuwa gidan ne, anya ma kuwa HAMDAH suka gani a TV ko dai idanunsu ne ke yi musu gizo, ko dai wata ce me irin sunan ta suka gani suke tunaÉ—in É—iyar su ce?. kai ta jinjina yayin da jikin ta ya É—anyi sanyi da tunanin afili ta furta "Sai na ga wannan É—in idan na tabbatar da ba ita ba bace sai na tafi na cigaba da niman ki HAMDAH." a hankali ta karaso bakin get É—in ta kwankwasa har sau uku, kana mai gadi ya taso ya buÉ—e karamar kofa ya leko kansa yace "Wane ne?." tace "Nice." yace "Gurin wa kika zo?." tace "Gurin HAMDAH." É—an shiru yayi kana yace "Tasan da zuwan ki ne?." Ummi tace "Bata san da zuwa ta ba." yace "To ba a bamu masaniyar cewa wata zata zo ba ki nimi izinin shiga kafin idan aka sanar mana sai ki shigo." yana kokarin mai da kofar yarufe tayi saurin cewa "Dan Allah kace mata Mamar ta ce ta zo." yace "Maman ta haba Hajiya mun saba jin irin wannan." ya mai da kofar zai rufe da sauri tamaso bakin kofar tana faÉ—in "Ganin ta kawai zan yi idan ba ita bace bama ni zan tafi." wani security ne ya mike daga in da yake zaune ya zo bakin kofar yana faÉ—in "Mene ne wa tazo gurin sa?." maigadi yace "Wai gurin Hajiya ta zo wai ita mamar Hajiya ce, nace mun saba jin irin wannan masu neman taimako su rika fakewa da Æ´an uwan ta ne sai sun shiga kaji babu abin da ya haÉ—a su." jami'in tsaron yace "Ita ta gayyaci ki ina katin shaidar." Ummi tace "Bata san da zuwa ta ba kuce mata mahaifiyar ta ce tazo." sauran security suka mike daga in da suke tsaye cikin faÉ—a suka ce su rufe kofar takira a sanar musu tukun abar ta ta shigo. maigadi ya rufe kofar. yana faÉ—in "Mutane babu godiyar Allah kaduba wannan matar kwata-kwata batayi kama da mabukata ba amma hali irin na mutum kabari a bawa na kasa da kai wai kai ma sai ka nimi kari." Faty da ta fito daga side É—in su zata je gidan makotan su gurin kawarta, ta nufo bakin get tana hango yan da security suke magana da faÉ—a-faÉ—a da alama dai da wani wanda ya nimi shiga gidan suke, ta karaso bakin get É—in, mai gadi ya mike ya buÉ—e mata get tasa kai zata fita, sai ta hango Ummi a tsaye a gefe tayi jigum. sai ta leko tace wa maigadi "Wace ce wannan É—in?." mai gadi yace "Wai gurin Hajiya tazo kuma mu Hajiya bata bamu masaniya kan cewa wata zata zo ba, wai cewa tayi ita mamar Hajiya ce." Faty ta dube ta kana ta karasa fita waje." kana mai gadi ya mai da kofa ya rufe. har Faty tazo zata gota ta sai ta ce mata sannu. Ummi ta amsa da yauwa, kana ta wuce. Ummi kuwa gefe da get É—in ta nima guri ta zauna, a ranta take ayyana bazata tafi ba har sai taga wannan HAMDAH'N idan ba HAMDAH'N ta nane sai ta tafi... Har Faty ta gama zaman ta gurin kawar ta tafito lokacin yamma tayi sosai, tayi mamakin gani matar nan har lokacin zaune a gurin. har tazo bakin get zatayi knocking sai ta juyo ta dubi Ummi daÉ—an fuskantar tausayi ganin ta zauna shiru, tace "Wai wa Adda HAMDAH kika zo gurin ta." da sairi Ummi ta juyo tare da gyaÉ—a mata kai, Faty tace "To ki kirata ki sanar mata kina bakin get zata sa mai gadi ya barki ki shigo, in ba haka ba security baza su barki ki shigo ba." Ummi tace "Bani da lambar ta, amma dan Allah kice mata mamar ta ce ta zo." kai Faty ta gyaÉ—a da mamakin matar jin tace wai ita mamarta,ita kuma wannan kalar nata salon kenan ko ba komai in ta faÉ—i haka ai za'a barta tashiga, gata kuma zubin ta baiyi kama da irin masu zuwa suna karyace-karyacen nan dan a barsu su shiga cikin gidan ba. kai Faty ta jinjina. sai tayi knocking maigadi ya buÉ—e ta shige ciki. Ummi ko zama ta kuma gyara wa. ganin lokacin sallar magriba saura kaÉ—an ga unguwar shiru babu ko motsin mutane, tun da ta zauna ita dai bata ga wani mutum yazo ya wuce ba sai dai motoci É—ai-É—ai su zo su wuce, unguwar shiru kamar babu bil'adam, sai sautin kukan karnukan gadi. a hankali Ummi ta mike tazo jikin get É—in ta kwankwasa. mai gadi ya buÉ—e ido ya waro yace "Har lau kece?." a fusace security suka tambaye sa waye? yace musu "Matar É—azun É—in nan ce." a fusace É—aya daga cikin su ya mike yafito yace mata maza-maza ta bar bakin get É—in nan tayi nesa da gidan nan tun bai sa bindiga ya harbe ta ba, ya É—aga bindiga yana faÉ—in tayi sauri ta bar eriyan nan. ai ko da sauri ta É—au jakar ta tasoma tafiya, cike da takaicin wai ita ce ake yiwa korar kare irin haka, amma babu komai zata jure koma mene ne har idan zata samo É—iyar ta... Acikin gidan kuwa Faty na zaune a parlour ganin Bappa ya mike yana faÉ—in "Lokacin salla ya kusa bari na shiga Masallaci." da sauri ta mike tace "La na mance wata mata tun É—azu ta zo tana bakin get security sun hanata shiga, wai cewa tayi ita mamar Adda HAMDAH ce, na mance naje na faÉ—a mata ko zata sa a barta ta shigo wata kila taimako ta ke nima." tsayuwa Bappa yayi kana yaÉ—an yi shiru yace "Tace ita maman ta ce?." kai ta gyaÉ—a tana mike wa da faÉ—in "Bari naje na faÉ—a mata Allah ta ban tausayi tun É—azu take zaune a waje." Inna Wuro tace "To shine tun tuni baki je kin faÉ—a mata ba kika zauna shiriri ta, ace tunruni tana waje ai ko kuÉ—in mota aka bata zata ji daÉ—i." waje Faty tayi tana faÉ—in "Yan zu zanje na faÉ—a mata ai wata kila har yanzu tana waje dan ko shigo wa ta ma a waje na barta." Ina daga parlour'n sama najiyo muryar Faty a parlour'n kasa, Ahmad na zolayar ta budurwar Ustaz tana ce masa ita bata ma sanshi ba, ta hayo saman tana dariya. na sako kai na zan sauko ita kuma zata shigo parlour'n sama tace "Yauwa Adda HAMDAH dama gurin ki zan je, tun É—azu wata mata tazo tana bakin get security sun hanata shiga tace wai ita mamar ki ce, su kuma suka ce karya take so take abarta ta shigo kawai." ido na waro tare da dafe kirji nace "Wai ita mama tace?." kai Faty ta gyaÉ—a min. da sauri nace "Tana ina?." tace "Tana bakin get." da saur na wuce ta ina faÉ—in "Ina so na ganta babu wan da ta taÉ“a zuwa tayi karyar cewa ita mama na ne, sai dai suce su Æ´an uwa na ne, ina so na ganta." nayi maganar ina karasa sauka daga step da sauri, gaba É—aya jikina ya É—au kyar ma, cikin hanzari na nufi kofa da sauri haÉ—e da sassarfa nayi waje. da sauri Ahmad ya mike rungume da Ahmad karami yana tambayar Faty ta faÉ—a masa ko mene ne, bayan na yabi da sauri su Naseem suka biyo sa... tun daga farfajiyar gidan naÉ—aga murya ina faÉ—in "Mai gadi ina matar take." har na karaso get É—in, da sauri msi gadi ya mike yace "Hajiya an kore ta ta tafi." murya a hargitse nace "Kuje ku kira ta yan zu ku dawo da ita ina so na ganta." cikin hanzari biyu daga cikin security sukayi waje suka lelleka kana suka dawo suka ce, basu gan ta ba. ganin yan da gaba É—aya lokaci guda na ruÉ—e cikin tsawa Ahmad yace "Kuje ku nemo ta yanzun nan kuzo da ita." ai ko da sauri sukayi waje. niko tsayuwa na gyara ina mai da numfashi kamar wacce tayi tsere. Bappa ya karaso in da muke yana tambayar matar ta tafi ne?. Ahmad ne ya iya bashi amsa nikam gaba É—aya na ruÉ—e sai kyarma nake haka kawai naji ina so na ganta. munkai tsawon minti 15 tsaye a gurin kafin aka turo kofa, ganin security ne yasa ni É—aga murya nace "Ina take?." yace "Gata nan Madam sai da muka fita can farkon eriya kafin muka iske ta." yayi maganar ne yana shigo wa ciki, niko leken bayan sa nake ina alla-alla naga matar. a sannu ta sako kafar ta cikin gidan da sallama yayin da É—ayan security ke biye da ita. kamar almara kamar a mafarki nake binta da kallo yayin da na wawwaro idanuna waje cikin matukar mamaki. ido na kuma waro wa da karfi na furta "Ummi Ummi na!!." da gudu nayi in da take na rungume ta ina faÉ—in "Ummi dama kece Ummi kece." sai kawai na fashe da kukan farin ciki ina daÉ—a rungume ta. ita ma rungume ni tayi tana bubbuga baya na yayin da hawaye ke zuba a idon ta tana faÉ—in "Kiyi hakuri HAMDAH kiyi hakuri........! 8/19/22, 10:58 - Ummi Tandama😇: 33 Bappa ya soma da addu'a bayan addu'a ya É—aura da faÉ—in "Alhamdulillah muna godiya wa tabakara maÉ—aukaki mabuwayi mai izza, wan da ya nuna mana wannan rana, muna niman tsari da sharrin masu sharri Allah ya kaÉ—e mana fitina, muna godiya wa Allah da ya nuna mana wannan rana, Allah ya daÉ—a kaÉ—e mana fitina duniya da kiyama." kowa ya amsa da amin amin, Bappa ya gyara zama tare da ci gaba da faÉ—in "Abubuwa sun faru da dama bama fatan hakan ta kuma faruwa Allah ya kaÉ—e fitina, ya iyar mana abun da baza mu iya ba, Allah yayi mana maganin makiya da masu hassada kamar yadda ya nuna musu karshen sharrin su, hakika addu'a makarin Mumini ne, a na son musulmi a duk in da yake a duk halin da yake ya kasan ce mai ruko da addu'a, domin addu'a takwabi ne mai kaifi ya kan tsare fitina da sharri da kaifin sa, hakika wannan abu da ya faru ya nuna É—an dakacin addu'a kaÉ—an duk da Allah yayi taimako an farga da wuri, Allah ya da É—a tsare mu ya yi mana katangar karfe da azzalumai." Abbu ya jinjina kai cike da gamsuwa yace "Amin ya rabbil izzati, hakika addu'a takwabi ne mai kaifi hakika lamarinnan ya jijjiga mu ba kaÉ—an ba duk da bakin mu baya iya furta wa amma zuciyoyin mu tana kuna." ya É—an sakai ta maganar tare da duba na kana yaci gaba da faÉ—in "Kiyi hakuri HAMDAH duk da bamu kuma yunkurin niman ki ba amma zuciyoyin mu suna tare da ke a ko da yaushe." kai Bappa ya jinjina dan ya san cewa ai kin sihiri kenan shi yasa ake so a koda yaushe mutum ya zamana yana cikin sarki da addu'a idan aka jefe ka da shi bazai yi wani tasiri a tattare da kai ba... Abbu yace "Muna mai ci gaba da baki hakuri hakika mun ai kata rashin kyautawa wa rayuwar ki, a matsayin mu na iyayen ki da kike da hakki a kanmu da muka gaza sauke shi na wasu shekaru mu na ruko da ki yafe mana." da sauri na shiga girgiza kai yayin da hawaye ke zuba a ido na kwalla na share nace "Abbu bakuyi min komai ba, Abbu ka rokar min Abba ya yafe min dan naga kamar har yanzu bai yafe min ba amma wlh ni ban taÉ“a ai kata zina ba." wani kuka ne ya tsuÉ“uce min na fashe da kukan, Aunty Rafee'at ta rungume ni itama ta fashe da kuka. cikin matuÆ™ar nadama Abba yake faÉ—in "Ki gafarce ni HAMDAH tsananin kunyar ki ce ta hanani iya furta komai, tabbas nayi danasanin yanke hukunci cikin fushi, ki gafarce ni ki gafarce ni HAMDAH ina mai da na sanin yanke hukunci cikin fushi, dana kore ki HAMDAH ina kika shiga ina kika shiga HAMDAH nayi da na sani nayi na dama HAMDAH ina kika je wani rayuwa kika yi?." Abba yayi maganar cikin nuna nadama sosai kamar zai zubda kwalla. in da yake na rarrafo tare da rike hannunsa gam kana a hankali nashiga basu labarin abun da ya faru, tun ranar da na sa kafa na bar gida da rayuwar da na fara fuskanta, da rayuwar da mukayi cikin daji ni da su Naseem da, irin gwagwarmayar da na sha a rayuwa har na kai matsayin da na ke a yanzu. tun da na fara bada labarin gaba É—aya parlour'n ya kacame da koke-koke su Aunty Rafee'at har da jan shassheka, Ummi Mamie gaba É—ayan su kuka suke wei-wei kamar kananun yara, Abba Abbu Bappa Ahmad duk kanin su sai sharar kwalla suke. Abba yana sharan kwalla yana faÉ—in na yafe masa, kai na shiga girgiza wa nace "Baka yi min komai ba Abba." Mamie tana kuka ta rungume su Naseem da tun É—azu take jin wani yanayi a kansu a kasan ranta take faÉ—in a she dai jinin ta ne su shiyasa tun da ta sanya idanunta kan su take jin su a cikin jikin ta. su Abbu suka shiga yiwa Bappa godiya da irin kokari da jajirce wa kan lamari na da yayi yake kuma kan yi shi da matar sa wato Inna Wuro. Bappa yace ai yiwa kaine, da É—a da dukiya bana mutum É—aya bane kuma ba'a yi musu keta. sun yaba kwarai da gaske da irin kokarin da Mama mai awara ta yi a kaina suka kuma É—au alkawarin niman ta suyi mata godiya. Ahmad ma godiya suka yi ta masa suka kuma yi jinjina ga Rasheedat matar da ba kasafai ake samun irin su a duniyar mu ba.... A É—aya side É—in da babu kowa ciki wan da yanzu su Talatu suke kwana ciki, nasa su Talatu suka fita suka koma side É—in su Inna Wuro suka shiga É—aya daga cikin É—akunan side É—in wan da ba kowa ciki, wannan side É—in kuma nayi wa su Abbu da Abba Ya Masa'ud Fauzan masauki ciki. É—aya daga cikin É—akunan kasa kuma aka shigar wa Mamie kayan ta ciki, É—aya É—akin kuma Aunty Jaleela da Aunty Rafee'at da Nusaiba. a ranar raba dare mukayi muna hirar bayan rabo da ahlina abu mafi soyuwa a rayuwa ta, Ahmad kuwa gidan sa ya tafi yace ya barni na gana da Æ´an uwa na, bayan ya gama zolaya ta wai na share shi na nuna masa wariya... kwanan su Abbu uku suka soma shirin komawa gida bayan na kaisu na nuna musu duk kanin kadarori na da suke cikin garinnan, sauran na wasu gararruwan kuma a computer na nuna musu.. ranar da suka cika kwana biyar suka juyo Bauchi, amma banda Ummi dan ta ce ita tana nan sai ta yimin zaman arba'in tukun. Abba ko da wasa bai yi yunkurin hana ta ba, sai dai ma karfafawa zaman nata da yayi, yace ta zauna tayi min wankan arba'in kamar yadda ake yiwa mai haihuwar fari dan na cancanci haka, duk da na sami ingantaccen kulawa gun Mama mai awara a haihuwa ta ta farko wan da ya kamata ace uwata ce ta bani wannan kulawar, to amma guri bai kure ba, ta zauna nakuma kara samu agurin mahaifiya ta... Ahmad yayi musu goma na arziki dan mota guda ce ta raka su da kayan tsaraba, bayan wan da nima nayi musu.. lokacin da suka iso gida Masa'ud ya shiga É—akin sa, yayi matukar mamaki haÉ—e da razana ganin SALEEM cikin É—akin a kwance ya dukunkune cikin bargo sai rawar sanyi yayi, lokaci zuwa lokaci kuma sai yayi wasu tagwayen tari ya dafe kirjin sa da karfi yana matse idanunsa. a bin da ya daÉ—a bashi mamaki shine kayan jikin sa, kayan da yazo da shi gidan ranar da zasu tafi Abuja gurin HAMDAH, "Kenan tun ranar yana É—akin nan?." Masa'ud yayi maganar a ransa, da sauri ya karaso bakin gadon yana faÉ—in "Subhanalla Ya SALEEM baka da lafiya ne?." da ido kawai ya bishi barate da yayi magana ba. ganin yan da ya kuma rumtse idanunsa yana daÉ—a damke kirjinsa, da sauri Masa'ud ya fito dan yaje ya sanar wa Mamie halin da SALEEM É—in yake ciki. a sakiyar gidan ya haÉ—u da su Abbu da alama masallaci zasu tafi, da sauri ya karaso in da suke yace "Abbu Ya SALEEM bashi da lafiya yana kwance a É—aki na." da sauri Abba yace "Subhanalla me ya same shi?." ya juya da sauri ya nufi É—akin nasa Masa'ud ya rufa masa baya. Abbu kam tsayuwa yayi yaÉ—an yi dimm kana ya girgiza kai yawucw masallaci abin sa.. Abba na shiga É—akin ganin halin da yake ciki yashiga tambayar sa abin da ke damun sa, ba wani kwakkwaran amsa ya samu a gurin sa ba dan tun da ya tambaye sa, me ke damun sa ya nuna masa kirjin sa bai kuma cewa komai ba duk tambayar da yake masa. Abba ya É—aga waya ya kira Dr Farooq yace ya zo yanzu. batare da É“ata lokaci ba Dr Farooq ya iso. bayan sudduba shi da yayi ya rubuta masa magani, Abba ya bawa Masa'ud kuÉ—i yaje ya siyo maganin ya kawo masa.... Abuja Ina samun kulawa sosai wajen Ummi na, dan dole Ahmad ya tarkasa ya koma gidan sa sai dai yazo ya duba mu ya koma. yanzu bani da wata damuwa a rayuwa ta hankali na ya daÉ—a kwanciya, na daÉ—a yin É“ul-É“ul da ni na kara haske da sheki na kara kyau, kullum ina tare da Ummi na hankali na a kwance.. Hajiya Lubabatu na kira nayi mata aiken kuÉ—i ta turo min kayan gyara irin na masu jego. kafin na cika arba'in kuwa idan ka ganni sai ka kara kallo na, shi kan sa Ahmad idan yazo yakan zauna ne yata kallo na, wai shi ya godewa Allah da ya kawo masa Ummi tamkar kara min kyau take, dariya kawai na ke masa. ranar dana ciki arba'in Ummi ta fara shiri washegarin ranar Ummi tace yau ba kwana sai Bauchi, na sha kuka na har na gaji, nace sai dai mu tafi tare, tace a'a na bari sai jiki na ya daÉ—a karfi jaririn ma yadaÉ—a kwari sai nazo zan fi jin daÉ—in zuwan... direba ya shirya kayan ta cikin mota da kayan tsarabar ta da Ahmad yayi mata, da wan da nima nayi mata. muna tsaye a parking space dukan mu gudan sai hawaye nake sharewa, cikin tura baki nace "Allah Ummi sati É—aya zan kara na zo." tace "A'a HAMDAH kibari É—an nan ya daÉ—a yin kwari kada kirika kwasar sa kina yawo da shi bai yi kwari ba, kibari nan da wata uku lokacin yayi kwari sosai sai ki zo." ido nawaro nace "Ummi har wata uku Allah ni dai a'a." Inna Wuro tayi murmushi tace "To in ban da abin ki HAMDAH wata uku yanzu nawa yake kamar gobe ne agurin Allah." Ahmad kuwa sai washe baki yake adole yaji daÉ—i an ce ba yanzu zan tafi. Ummi ta shige mota direba ya ja muna É—aga mata hannu har suka fice daga gidan. na juya jiki a sanyayi cike da kewar ta... ina shiga parlour Ahmad dake biye da ni ya rungume ni ta baya, baki na turu gaba ina yi masa hararar gefen ido. murmushi mai sauti yayi kana, ya cusa fuskarsa a gefen wuyana na ya sumbaci fatar wuyana a hankali yaÉ—an ja numfashi yace "Kyakkyawa ta yaufa a shirya shirin karÉ“ar bakwanci na." baki na kuma turo wa tare da fizge jikina nace "Ni ka kyale ni." dariya yayi cikin zolaya yace "Zo muje oh na rarrashe ki Ummi ce ta hana ki tafiya ko?." baki na murguÉ—a nace "Ina har murna kake." yace "Allah sarki Ummi Allah ya tsare miki hanyar ki, taji tausayin Ahmad da Ahmad shi yasa tace ki kula da su kafin, muje a fara bani nawa kulawar yanzu." kafa na shiga bubbuga wa, ya janyo hannuna muka haura sama yana dariya.. Bayan sallar isha, tsaye nake gaban mirror ina feshe jikina da turare bayan fitowa ta daga wanka, Ahmad ya shigo ya iso ya rungume ni ta baya, daga cikin mirror ya kura min ido yayin da ya sako kan sa kan kafaÉ—a ta yana yimin kallon cikin ido, sanin manufar sa sai na É“ata fuska na zame jiki na ina tura masa baki. murmushi mai sauti yayi ya ruko ni yana faÉ—in "Wai ba É—azu nayi rarra shin nan ba to zo na kara yanzu kam na Musamman ne, shi yasa nasa su Naseem sukayi bacci da wuri." cak ya É—aga ni ya dire ni kan gado, ganin ya shiga zare kayan jikina da sauri nace "Ban fa warke ba ni dai ka bari." sai da ya zare doguwar rigar baccin jikina kafin ya É—ago har jikin sa na rawa yace "Please kyakkyawa ta, kwanaki arba'in da Æ´an kai kiji tausayi na mana." cike da shagwaÉ“a nace "Allah My zafi zai min kamar bai warke ba." yace "To bari na gwada na gani idan bai warke ba sai na hakura, a hankali zanyi kinji ki daure." kai na gyaÉ—a masa, har jikin sa na É“ari yashiga shafari da sumbatar sassan jikina, ya birkice ya birkita ni sai na shiga mai da masa martani. sai da ya jagula ni na jiku sosai kafin ya É—ago ya zare pant É—in jikina, nan ma sai da yayi ta wasa da HQ É—ina kafin ya haye kaina. idanuna na rumtse san da ya shige ni da tunanin jin zafin gurin É—in kin da a kamin, sai naji akasin hakan. tamkar yau yafara sanina haka yayi ta sambatu yayin da yake ta sama da kasa a kaina. ya sharin tsawon lokaci mai tsawo a kaina yana abu guda, nayi ta daure wa domin ganin ya sami nutsuwa dan nasan yayi missing É—i na sosai. sai da ya sami ingantacciyar gamsuwa kana yayi lamo a kaina, duk kanin mu numfashi muke sauke. a hankali ya É—ago yayi kissing É—in goshi na yace "Nagode sosai kyakkyawa ta Allah yayi miki albarka." idanuna na lumshe tare da kuma buÉ—e su kan fuskarsa tare da yi masa murmushi, shima murmushin ya maida min kana yace "Ina son ki kyakkyawa ta." a hankali ya zare jikin sa ya mike ya É—ago ni muka shige bayi..... washegari da safe ina manne da waya a kunne na muna waya da Ummi, Fauzan ya karÉ“i wayar muka gaisa da shi. ina kashe kawar Ummi, kiran Mamie na ahigo wa waya itama sai da muka gaisa har da Nusaiba, dan tun da suka koma kusan kullum sai munyi waya da su har..... Bauchi a É“angaren Na'ima kuwa tana zaune cikin bedroom É—in ta waya ce kare a kunnen ta tana magana da aminiyar ta Raliya, tana faÉ—in "Aminiya nikam anya bokan nan ai kin sa na ci kuwa, nifa banga yan da ake ta faÉ—a kamar yankan kuwan ba, gashi bini-bini sai yace abada dubu É—ari kaza miliyan kaza kin san har account É—i na yafara yin kasa kuwa, ba wannan ba ma ban damu da koda kuÉ—in zai kare idan har zan sami biyan bukata duk abin da na mallaka zan iya É“atar da shi har idan za'a kashe wancan shigiya annobar yarin yar, dan wlh ta zame min annoba, jiya muna kwance da shi da daddare yana bacci yana kiran sunan ta, kin yanzu baya fita ko offece kullum yana É—aki, daga zaran bacci ya É—auke sa zai fara kiran sunan ta, idan naji haushi na bubbuga shi ya tashi yana farka wa zai ruko ni yana faÉ—in HAMDAH, ke Aminiya ina cikin babbar matsala dan Allah yanzu muhaÉ—u agurin boka ai, ko nawa yake so na kara masa ni zan basa, nifi son ai kin da za'a yi sha yanzu maganin yanzu, bana son ai ki mai jinkiri shi yasa nake son ai kin boka na kan dutu, ban so mutuwar sa ba da yana nan da duk haka bata faru ba, dan Allah aminiya mu haÉ—u yanzun nan gidan boka gani nan fitowa." ta kashe wayar ta mike ta zari mayafin ta da makullin mota tayi waje. SALEEM na zaune gurin hutawar sa ya hango ta ta shige mota tayi waje, da ido yabi ta har tayi waje, a zahirin gaskiya kuwa hankalin sa ba ya tare da shi, ya milla yayi nisa daga gare sa, a hankali ya kai hannunsa ya dafe kirjin sa yayin da ya fara tari a hankali babu kakkautawa. wani irin zafi da zugi zuciyar sa yake masa, a hankali ya mika hannu yaÉ—au É—aya daga cikin wayoyin sa da suke aje kan table É—in gaban sa wan da ya É—aura kafafun sa a kai, yayin da hannunsa É—aya ke dafe a kirjinsa. Dr Farooq ya kira bayan sun gaigasa yake Dr Farooq yake tambayar sa yaya jiki?. bai amsa tambayar ya jikin da yayi masa ba sai cewa yayi "Ka faÉ—a min sunan wani maganin da zan sha." Dr Farooq yace "Wan can É—in baiyi maka amfani bane?, to gaskiya kazo asibiti kawai zai fi a duba ka da kyau a baka magani, Please Ya SALEEM ka zo yanzu." bai yi magana ba sai sauke wayar da yayi a kunnen sa, a sannu ya mai da bayan sa jikin kujera tare da lumshe idanunsa har lokacin hannunsa É—aya na dafe a kirjin sa. Dr Farooq yakira sa har sau biyu bai É—aga wayar ba, yana jin wayar tana vibrate bai ko buÉ—e idanunsa ba. sai da yaji alamar shigowar message kafin ya buÉ—e lumsassun idanunsa ya É—au wayar yana duba sakon da ya shigo masa, Dr Farooq ne ya ai ko masa da sakon cewa dan Allah yazo asibiti kada ya É“ata lokaci. bayan da ya gama karanta sakon sa sai ya mike ya kwashi wayoyin sa yanufi side É—in sa. sai da yayi wanka ya shirya kana ya É—au makullin motar sa ya nufi asibitin, ko da ya iso asibitin. bayan tambayoyin da Dr Farooq yayi masa kan ciwon nasa, Æ´an takaitartun amsoshin da ya basa da shi yasamu damar yi masa gwaji kan abun da yayi hasashe bisa amsoshin da ya basa.. lokacin da Dr Farooq yaga result É—in test É—in ya jijjiga ba kaÉ—an ba, ganin yana daf da kamuwa da ciwon zuciya, hankalin sa a matukar tashe yake basa wasu shawarwari kan yan da zai gudanar da lamuran sa domin gujewa kamuwa da ciwon zuciya, ya tausaya masa kwarai da gaske, ya É—aurasa kan magani. har gurin motar sa ya rako sa ya, yana daÉ—a jaddada masa yan da zai kula da shan maganin sa, SALEEM yana kokarin shiga mota Dr Farooq yakuma duban sa yana faÉ—in "Dan Allah Ya SALEEM ka kula da shan maganin ka, kuma dan Allah ka rage tunani idan Allah ya tai maka zai tsaya iya haka Allah ya sauwaka." ya amsa da amin kana ya shige mota... A É“angaren Na'ima kuwa zaune suke a gaban sabon bokan su, sun naÉ—e kafa gaban sa kamar masu niman gafara, sun kura ido suna kallon yan da yake ta wani surkullen sa, yayi zane kan kasa ya bubbuga ya share ya kuma zana wa. bokan ya É—ago ya dube su yace "Zata mutu mutuwar wulakanci amma aljanun da zamu tura su sun ce suna bukatar jini rakuma kosassu guda goma kafin suje suyi ai kin." kirji Raliya ta buga tace "Rakuma guda goma kosassu ayanzu fa kuÉ—in ko wani É—aya zai kai miliyan uku." bokan yayi wani irin dariya yace "Bazaku iya ba ku tashi ku tafi." da sauri Na'ima ta gyara zama tace "Boka zamu iya." wayar ta ta É—aga taduba balance É—in account É—in ta taga babu wani yawa sosai dan duk ta gama basa kuÉ—in. ta yi masa transfer É—in duka kuÉ—in zuwa account É—in shi, kana ta aje makullin motar da tazo da shi a gaban sa tace "Asai da motar a haÉ—a da kuÉ—in idan basu kai ba zan nemo cikon, ni dai dan Allah boka ayi min kokari bana so a sami matsala, a iashe ta kawai shine samin kwanciyar hankali na, ko bacci mai daÉ—i bana samu yanzu." boka yace "An gama mabi da matsala yau za'a sai da motar idan kuÉ—in ya cika, da daddare za'a bawa aljanu jinin rakuman a daren nan zasu kashe tai, dan kuma bai cika ba zamu neme ku." suka mike suna ta zuba masa godiya a motar Raliya suka fito saga cikin dajin.. suna tafe Raliya ta juyo ta dube ta tace "Aminiya amma yanzu idan boka yace a kawo ciko a ina zaki samu cikon?." Na'ima tace "Agurin SALEEM ai da ma daga gurin sa suke fita, zan sa a É—auke Ameer a nimi kuÉ—in fansa a gurin sa dai-dai kuÉ—in siyan rakuman, idan ya bayar sai na bawa boka cikon kuÉ—in narike sauran." dariya Raliya tayi tace "Kai Aminiya daÉ—ina da ke kwakwalwar ki na ja, idan aka sace É—an sa kam ai da gudu zai kawo kuÉ—in babu gargada." Na'ima tayi wani murmushi mai cike da tarin makirci.... Abuja Kullum a cikin lissafin tafin watannin ukun da Ummi tace na kara kafin nazo nake, sai nake ganin lokacin yayi min nisa. da kyar naga wata biyu yayi. kullum idan muka yi waya da Ummi sai na ce mata Allah Ahmad yayi wayo sosai yayi kwari nace kuma bari taji dariyar sa, sai nayi ta masa wasa yayi ta kyalkyalewa da dariya nace taji shi ko. tace taji amma dai na bari na cikita wata É—ayan tukun.. idan Ahmad yaji muna waya da Ummi yarika yimin dariya kenan sai yace wai Ummi ta fiso na zauna na kula da su.. ranar da wata É—ayan nan ya cika, tun da na farka da asuba ban kuma iya komawa bacci ba, a kwatunan kayan mu na sauke waÉ—an da na shirya su tun sati É—aya daya wuce. ranar Ahmad baya gida na, na kira sa a waya nace kasa mu fa mub gama shiri, yace na jira sa gashi nan zuwa. ina zaune a parlour ya shigo su Nasmah suka rungume sa suna yi masa oyoyo, sai da ya É—aga ko wannen su sama kafin ya dire su yana bin su da dariya. in da na ke ya karaso ya É—auki Ahmad karami dake kan kafata yarika cillashi sama yana kwalkwale dariya, ganin yan da ya shagala da wasa da yaron yana kuma biyewa su Naseem da suke taya sa wasa wa yaron, na turo baki gaba nace "My rana fa zatayi kana so muyi tafiyar dare ne." zama yayi gefe na tare da manna min kiss a kumatu yace "Kyakkyawa ta ki bar tafiyar nan yau." ido na waro nace "Me ne!?." janyo keken da ake saka Ahmad karami a ciki yayi yasaka sa ciki kana ya tura sa gefe ai ko da gudu su Naseem sukayi kansa suna yi masa wasa yana ta É“alle musu da dariya. janyo ni jikin sa yayi ya sakalo hannayen sa ya zagaye ni da shi, a hankali cikin tattausan lafazi yace "Ki saurare ni kiji abin da zan faÉ—a, ai tafiyar ba naki ke kaÉ—ai bace har da ni da su Bappa,jibi ina da wani zaman da zamu yi kuma mittin ne mai muhimmanci, nayi miki alÆ™awari idan mukayi mittin jibi washegari zamu tafi." kai na langwaÉ“ar gefe zan yi magana yace "Kar kice komai kika iya jiran wata uku kwana uku ne zai gagara iye kyakkyawa ta?." yadda yayi maganar a marairaice tare da langwaÉ“ar da kansa gefe, sai ya bani dariya murmushi nayi nace "Amma Allah kwana ukun nan kam idan yazo babu fashi." yace "In Allah ya yarda." kai na girgiza nace "To Allah ya kaimu." daÉ—a rungumo ni yayi yana faÉ—in "Amin Amin." ganin yana shirin haÉ—e bakin mu nayi saurin kawar da kaina gefe, nace "My yarannan fa suna nan." ido ya kashe min yace "Su da suke wasan su hankalin su baya nan." fuska ta ya juyo tare da haÉ—e bakin mu, idanunsa a kan yaran garin hankalin su na kokarin dawowa kanmu sai ya zare bakin sa ya sake ni, ya mike yana faÉ—in "Kuzo muje musha ice-cream." ya É—auki Ahmad karami ya dube ni yace "Madam muje ko." a sannu na mike kasan cewar da mayafi a jikina muka nufi gurin mota. ya buÉ—e wa su Naseem gidan baya suka shiga, kana ya mai da marfin ya rufe sannan ya matso ya buÉ—e min gefen mai zaman banza, sai da na shiga kafin ya miko min Ahmad karami. kana ya zaga ya huÉ—e driver seat ya shiga, yana kokarin ta da motar da sauri wani security ya iso,yaÉ—an leko gefen da nake cike da girmamawa yace "Barkan ku da warhaka." Ahmad ya ce yauwa, yace "Madam dama wata ce ta zo, wai tazo niman taimako ne ansan da zuwan ta ne." kai na girgiza nace "Okay bari idan muka fita wajen sai a taimaka mata." yace to ya juya da sauri mai gadi ya wangale get muka, Ahmad ya ja motar muka fito a hankali. matar tana É—an rakuÉ“e a gefe kallon ta nayi saga sama har kasa, gaba É—aya kayan jikin ta sun koÉ—e hatta hijabin jikin ta tagefe duk a yayyage, silifas É—in kafar ta ya cinye kusan rabib kafar ta a kasa yake, tana rungume da bakko a hannunta. Ahmad yayi hon da É—an sauri ta nufo in da muke, ido na kurawa matar, da sauri na kai hannu na mussuke idanuna da kyau na zuba su a kanta, dai-dai lokacin da ta karaso jikin motar tagefen da nake tana faÉ—in "Alhaji Hajiya a taimaka min da ko kuÉ—in mota ne na koma garin mu." wani irin waro ido nayi da karfi na furta "Mama!". ta É—ago da sauri ta na duba na, juyo wa nayi gun Ahmad ina faÉ—in "My ita ce Mama mai wara ita ce wlh." sai kuma na juyo in da take ganin tana bina da kallon rashin sani nace "Mama baki gane ni bane nice fa HAMDAH ce fa Mama." da sauri na É—ago Ahmad karami na É—aura kan kafar Ahmad na buÉ—e marfin motar da sauri na fita. ido ta kura min tana nuna ni da yatsa murya na rawa tace "HAMDAH kece HAMDAH kece haka ke kika zamo haka HAMDAH?." rungume ta nayi a tare muka fashe da kuka cikin muryar kuka nace "Nice Mama, Mama nayita niman ki har na É“ata." ita ma tace "Nima nayi ta neman ki HAMDAH ashe darabon ganawa." Ahmad ya fito daga cikin motar, na sake ta tare da share hawaye na na nuna mata shi nace "Mama miji na ne shi." murmushi tayi tana share hawaye tace "Shine SALEEM?." kai na girgiza mata. Ahmad da take ta binmu da murmushi yace "Sannu Mama." tace yauwa. tace "Ina Naseem da Nasmah?." nace "Gasu nan cikin mota." Ahmad ya buÉ—e musu suka fito na kamo hannun su na kawo su gaban ta nace "Ga Mama wacce tasha É—awainiyar ku tun kuna ciki." hannunsu ta ruko tana faÉ—in "Masha Allah Naseem Nasmah kune kuka girma haka." Naseem da ya washe baki yace "Ai Daddy yace mun gima ga kanin mu a hannun Daddy ni Yaya Naseem ne." dariya dukan mu kayi, Mama ta dubi Ahmad karami da ke rike a hannun Ahmad sai washe baki yake kamar wan da yasan abun da ake faÉ—a, tace "Masha Allah kanin ku kenan yaya sunan sa?." Nasmah tace "Ahmad." nace "Mama mu shiga ciki." tana rike da hannun su Naseem muka shige cikin gida, Mama ta rika bin katafaren gidan da kallo tana jinjina kai. a parlour'n kasa muka zazzauna, Ahmad cikin girmamawa yashiga gaishe ta da taya mu murnar kuma haÉ—uwa, ya dube ni yana murmushi yace "Yau maganar Mama ya kare ko." dariya nayi ina É“oye fuska ta a jikin ta. kira ce ta shigo wayar sa ya mike yafita yana faÉ—in sai ya dawo. da kaina na fita naje side É—in su Bappa na sanar musu da zuwan Mama mai awara. a tare muka shigo parlour'n da su. sunyi farin ciki kwarai da gaske haÉ—uwar mu da ita, cikin yanayin damuwa Mama ta dube ni tana faÉ—in "HAMDAH ke da na ce miki ki jira ni ina dawowa shine kika tafi." nace "Mama nayi ta jiran ki da banga kin dawo ba shine nace zan biki kawai, a hanyata na tafi Yola na shiga motar É—an yankan kai." ido Mama ta ware tabuga kirji tace "ÆŠan yankan kai kuma?." kai na gwaÉ—a kana asannu na shiga bata labarin abun da ya faru daga lokacin da na shiga motar É—an yankan kai É—in nan har zuwa rana mai kamar ra yau. mama ta rika hawaye cike da tausayawa halin da muka shiga bayan ta, da ga bisa ni kuma tarika murmushi jin nasarorin da na samu bayan wuyan da muka sha. nace mata na zo Jos domin neman ta wacce nake da tabbacin zan sami labarin ta wajen su wato Zainabu da mijinta Malam musa mai maganin macizai, na tarar da sun tashi a gidan dan dana sansu. Mama tace "Nima lokacin da nadawo dan da É—auke ki mu tafi na tarar da bakya nan, nayi tunanin naje Bauchi ko kin koma gun iyayen ki ne, nayi tunanin ban san ta in da zan fara niman ki ba tun da bakara min gari bane, haka na koma Yola nayi ta rayuwar kunci É—an gonar gado na da nake gadara da shi matar yaya na ta saida wai gadon Æ´aÆ´an ta ne." kwalla ta share kana ta cigaba da bani labarin rayuwar da ta fuskanta a can, da kuma abun da ya kawo ta ganinnan, tace niman ai ki tazo yau satin ta guda kenan, bata sami ai kin ba duk gidan da ta shiga wasu su kore ta wasu kuma suce basa bukatar Æ´ar aiki suna da su, haka tayi ta kwana a kan titi shine ta fara yawon bara dan ta sami kuÉ—in mota ta koma Yola taje ta karasa rayuwar ta acan. rungume ta nayi tare da fashe wa da kuka, mukayi ta kuka. su Bappa ne suka yita bamu baki har mukayi shiru, kana Nappa yayi ta kwararo addu'a yace dama duk abun da yayi farko zaiyi karshe Allah ya tsayar mana haka. duk kanin muka amsa da amin amin, sai da sukayi hira sosai da Mama mai awara kafin suka koma side É—in su... É—akin da Ummi ta zauna na kai Mama nace tashiga bayi yayi wanka, tare muka shiga na nunnuna mata in da zatayi amfani da bathroom É—in kafin na fita. waya nayi a *HAM'NAS* Store Camplex nace a kawo min manyan dogayen riguna haÉ—e da atamfofi da mayafai da takalma marasa tudu, nafaÉ—i lambar takalmar da kuma adadin yawan kayan da nake so. batare da É“ata lokacin ba motar ShopRite É—in ta iso, da kaya niki niki cikin babbar jaka. na shiga da shi cikin É—akin da Mama take, lokacin har tayi wanka tayi salla tana zaune a kan sallaya, a gaban ta na aje jakar na zazzage kayan, na cire atamfofin gefe nace ta kwada dogayen rigunan ko zasu yi mata in basuyi ba aje a canzu. ta gwada zukayi mata Mama ta rika samun albarka tana hawaye. na kira tela yazo ya ganta kana ya É—ibi zannunwan ya tafi da su,bayan na sanar masa cikin kwana biyu nake bukatar su... muna zaune da Mama a parlour bayan mun gama cin abincin dare na kira Ummi bayan mungaisa nace "Ummu ga Mama mai awaran da nake faÉ—a miki wacce ta rike ni tamkar ke da kika haife ni." Ummi tayi ta murna tace na bata wayan su gaisa, nace to tare ma zamu zo. bayan sun gaisa Ummi tashiga zuba mata godiya, Mama tace ai ba ita kaÉ—ai bace Mama ta itama Mama ta ce. Ummi taji daÉ—i kwarai da gaske tayi mana fatan isowa Bauchi lafiya... bayan kwana biyu tela ya kawo É—in kin Mama, na haÉ—a na shirya mata wasu daga cikin kayan cikin É—an madaidaicin akwati.. Kamar yadda Ahmad ya faÉ—a bayan kwana uku motocin mu suka haura hanyan zuwa Bauchin Yakubu. motan mu daban ni da Ahmad da su Naseem duk muna baya in da direban sa ke janmu. motan su Bappa daban, Bappa na gaba shida direba Inna Wuro da Mama da Faty suna baya. har da su Uncle Mahmoud motan su daban shi yake jan motar sa da kansa shi da matarsa da Æ´aÆ´an su ne ciki dan shima yace ba za'a barsu a baya ba. sai motar security motar su guda, a hanya muka haÉ—u da su na fahimci biyo mu suke. a jere motocin suke tafiya, motan su Uncle Mahmoud ne a gaba na su Bappa na biye da su in da moton security ne ke biye da mu...... da misalin karfe uku muka iso cikin garin Bauchi, wani irin lumshe idanuna nayi tare da kuma huÉ—e wa a cikin garina mahaifata, na shaki iskar dake kaÉ—a wa ina mai farin ciki da jin daÉ—in gani na cikin garin. murmushi Ahmad yayi tare da jan kumatu na yace "Yarinya tana murna tazo kauyen su." dariya nayi nace "Nan É—in ne kauyen me Abuja yafi shi da shi." yace "Lalala birnin tarayya ne fa babu haÉ—i ai." nace "Ba wanin nan." yace "To dai nuna mana hanya ina zamu karmuje mu É“ata." dariya nayi tare da soma yi masa kwatance ya kira Uncle Mahmoud ya haÉ—a mu da shi narika yi masa kwatance har muka shigo unguwar mu. a bakin get Uncle Mahmood yayi hon mai gadi ya buÉ—e ya shiga muka bisa a bayan sa, a farfajiyar gidan motocin mu suka faka. numfashi mai karfi na sauke gani na a cikin gidan mu. su Aunty Rafee'at ne da su Mamie da Goggo Hauwa suka fito daga sashin Mamie da sauri suka nufo gurin motocin, da saauri na malle marfin motar na fito da sauri muka rungume juna cikin matukar farin cikin ganin junan mu, su Abbu suka iso gurin suna yi wa su Bappa sannu da hanya, kana a ka É—unguma aka shiga side É—in Mamie, security kuma aka shinfiÉ—a musu babban tabarma a gindin bishiyar anbulera dake gefe da tsakar gidan. muna zazzaune a parlour sai gaisawa ake, tuni Mamie ta sa su Aunty Rafee'at suka cike mu da kayan ci da sha wan da aka tanadar domin mu, aka É—ibi wasu aka kaiwa security. niko ina tsakiyar su Aunty Rafee'at da Aunty Jaleela da Ya Masa'ud, da Æ´an kanne na Nusaiba da Fauzan. Naseem da Nasmah suna like a jikin Ya Masa'ud wai har sun gane shi kenan sai surutu suke zuba masa, wannan yace Uncle kaza wannan yace Uncle. Ahmad karami kuwa yana hannun Mamie tana yi masa wasa yana dariya. ana ta hira cike da jin daÉ—i da nishaÉ—i. nan suka yi ta yiwa Mama mai awara godiya da irin kokarin da tayi a kaina... Acan gidan SALEEM kuwa labarin zuwan su HAMDAH ne ya iske Na'ima, a bujajan ta taso dan gane wa idon ta karya ne ko gaskiya, dan yau tayiwa boka alkawarin kawo masa cikon kuÉ—in sa, dan wan da suka shirya zai sace Ameer baya nan shine aminiyar ta Raliya ta bata aron cikiton kuÉ—in da zata bawa boka, idan aka karÉ“i kuÉ—in fansar Ameer ta biya ta, shikuma yayi mata alkawarin yau É—annan da daddare zai tura aljanu su kashe HAMDAH... Sallama muka jiyo daga sama, duk kanin mu muka mai da hankali bakin kofa, kamar an jefo ta haka ta faÉ—o cikin parlour'n, wani irin kallon-kallo muke yi da Na'ima da tayi mutuwar tsaye bakin kofa. dogon tsaki Aunty Rafee'at ta ja kana tace "HAMDAH kalli wannan hoton ki gani." tayi maganar tana nuna min hotunan mu da ta sa Fauzan ya É—ibo a side É—in Ummi. dariya nayi ganin hoton tun ina Dass wani lokaci Inna ta bani kuÉ—i naje na É—au hoton, kai na girgiza tare da faÉ—in "Allah sarki Inna ta." Ahmad da hankalin sa ke kanmu yana binmu kallon cike da sha'awa da burge wa ganin yan da muke da junan mu yace "Madam muga hoton." É“oye sa nayi a baya na ina dariya, Aunty Jaleela ne ta fizge hoton tana faÉ—in "Bashi yaga munin kawai." ta mika masa hoton. nace "Allah Aunty Jaleela ko a da ma na fiki kyau." Ya Masa'ud yace "Bare kuma yanzu har girma kin fita Æ´ar gidan Inna." dariya na fashe da shi nace "Yau wa Ya Masa'ud faÉ—a mata dai." Aunty Rafee'at tace "Oh Masa'ud zaka fara haÉ—in naka ko." tayi maganar tana dariya cike da kewar faÉ—ar mu da Aunty Jaleela da muka saba. Aunty Jaleela kuwa hararar sa tayi tace "Ni sa'ar ka ce Masa'ud?." Ya Masa'ud yace "Aunty Rafee'at matsa na mari bakin yarin yar nan." dariya muka yi dukan mu har da Ahmad da hankalin sa ke kanmu, yana kallon hoton yana dariya, idan muka haÉ—a ido da shi sai ya nuna min hoton yayi dariya, baki na rika murguÉ—a masa nima ina dariyar... Na'ima tana tsaye kamar wacce a ka kafata idanunta a kaina, kamar a mafarki haka take ganin komao. Ummi ce ta dube ta tace "Shigo mana Na'ima ya kika tsaya a gurin." ta janyo É—an da ke rike a hannunta suka karaso cikin parlour'n hankali a mugun hargitse.... Hospital Dr Mukhtar ne zauna cikin offece É—in sa, kamar daga sama yake jiyo hayaniya cikin asibitin, da sauri ya mike ya fito, sai ganin Æ´an sara suka yayi cike a cikin parlour'n asibitin shi, ko wannen su daga mai wuka sai mai adda sai walkiya suke, suna faÉ—in "Ina likitan yake." ido ya wawwaro cike da tsoro yace "Bayin Allah lafiya?." wani bakware ne yayi kansa da adda yace "Na sassare ka idan ka kuma mana tambayar da bata gamshe mu ba, kai ne likitan?." kai ya gyaÉ—a jikin sa na É“ari. yarinyar da suke tare da ita ya janyo ta yace "Kasan wannan?." Ido Dr Mukhtar ya kura mata yana ta son tuno in da ya taÉ“a sanin ta. mari É—an saran yayi masa da adda a fuska da karfi yace "Ka gane ta?." a gigice yashiga gyaÉ—a masa kai dan marin yasa shi tuno ta da sauri. yace "Eh..Eh.. na gane ta." murmushi bakwaren yayi yace "Ai da har na soma tunanin nasa yara su ankarar da kai su tsastsaga min kai." fuska bakwaren ya murtuke yace "Ina É—ana da ta zo ta siyar muku da shi anan, sabo da ku kananun Æ´an isaka ne shine zaku karÉ“i É—ana ku bata kuÉ—i, zan nuna muku naku iskancin kaÉ—an ne idan É—ana bai fito ba duk wan da yake da hannu kan lamarin sai na bubburma masa wuya." da sauri Dr Mukhtar yace "Wlh billahil lazi baya gurina yana gurin wata ne." kwashe sa wani yayi yakaÉ—a keyar sa yace "Wuce muje ka nuna mana in da take." suka tasa shi gaba suka É—aura shi kan mashinan da suka zo da shi, gidan su Raliya suka fara zuwa kasan cewar bai san gidan Na'ima ba. suka raki sa'a Raliya tana gida, yace musu da tare suka zo suka karÉ“i yaron shi bai san gidan ta ba ita tasan gidan ta. nan suka saka Raliya ita ma gaba bayan sun gama gwaza mata mari. suna zuwa gidan Na'ima mai gadi ya shaida musu ba ta nan, Raliya ta kira ta a waya tace mata tana cikin gidan su SALEEM, nan suka É—au hanyar gidan... koda suka zo shiga gidan ganin su da makamai sai security suka hana su shiga gidan... jin bayani ya a waje da karar wasa wukake da adduna yasa muka fito dan ganin me ke faruwa, jin abun da É—an saran nan yake faÉ—in "Wlh sai ya sassare ta idan bata fito masa da É—an sa ba." yasa Abbu cikin rashin fahimta yace wa security su bar sa shi ya shigo yaji gurin wa yazo." tare suka shigo da Raliya da yarinyar da yake ta janta, da kuma Dr Mukhtar. ido Na'ima ta cicciro cikin tsananin tsoro da firgicin ganin yarin yar da ta karÉ“i yaro a gurin ta tayi karyar cewa ita ta haife sa, ga kuma Raliya da Dr Mukhtar.. Abbu yace "Gurin wa kuka zo a gidan nan." bakwaren ya dubi yarinyar cikin muryar Æ´an iska da suka gama holewa da kayan maye yace "Bazaki nuna ta ba sai na daddatsa ki." da sauri yarin yar ta É—ago hannunta na rawa tashi nuna Na'ima tana faÉ—in "Gata nan ita ce wannan." baki ya karkata cike da rashin mutumci yace "Okay É—an nawa kenan wannan dan tsabar rashin daraja da kika san bazaki iya haifa ki rike ba shine bazaki kawo min shi ha, ance miki ni abin kunya dami na yayi zan kaiwa tsohuwa ta ta rike min shi, taho nan yaro nine ubanka." ya miko hannu zai ruko hannun É—an da ke hannunta. cikin rashin fahimta kowa ke kallon su Abbu yace "Me kake nufi kana nufin kace shi wannan É—an naka ne?.â€? yace "Eh mana É—ana ne mana." Abbu ya jinjina kai cike da al'ajabi yace "To É—an dakata kaÉ—an." wayar sa ya daddan na yakira lambar Ya SALEEM yana É—agawa Abbu yace "Duk in da kake duk abun da kake kabari yanzu yanzun nan kazo ina neman ka." daga cikin wayar Ya SALEEM yace "Gani nan kusa da gidan ma." yana kashe wayar mutar sa tana karaso wa nakin kofar gidan, ganin cincirindon kwarawa Æ´an tsara suka haÉ—e da hukuma a kofar gidan su, yasa shi fita cikin motar da sauri yanufi cikin gidan. yana sa kafa cikin gidan muka haÉ—a ido da shi. cak ya ja ya tsaya yayin da zuciyar sa tayi wani irin tsalle har sai da yakai hannunsa ya dafe kirjin sa da sauri. niko cikin hanzari na janye idanuna a kansa, yayin da naji kirji na yayi wani irin bugawa.. Abbu yace "Ka tsaya kuma ka karaso mana kai muke jira." a sannu ya shiga É—aga kafar sa har ya karaso gurin. Abbu ya dubi Ya SALEEM da kyau yace "Kasan wannan?." ya nuna É—an saran kai ya girgiza batare da yace komai ba. É—an saran cikin yanayin Muryar maye yace "Ai da ma bai Sanni ba, kamar yadda nima ban san shi ba, kamar dai yadda ban san wannan matar da ta siya É—ana ba." ya karashe maganar yana tangaÉ—e da É—aga addan da ke hannunsa sama yana nuna Na'ima da shi. Abbu ya girgiza kai kana yace "To kaji wai É—an ka É—an shi ne, dama nace kazo ya faÉ—a a kunnen ka bazai bamu sako mu faÉ—a maka ba." sai a lokacin Bappa yayi magana dan sai yanzu ya fahimci in da batun ya dosa, yace "Kai yaro kace É—an ka ne wannan ta ya aka yi ya zamo É—an ka bayan ga uba da uwan yaron anan?." mari ya kai wa yarin yar yace "FaÉ—a musu yan da kika yi kika siyar min da É—ana, a miko min shi na tafi ina da shara yau." duban ta Bappa yayi yace "Ke yarin ya ya akayi haka, da gaske É—an sane?." hawaye ta shiga share wa tana jan hanci tace "Eh É—an sa ne, dama..dama..dama lokacin ina da ciki ne da zan haihu shine iyaye na suka kore ni suka ce ba a gidan su ba, shine naje asibitin wannan." ta nuna Dr Mukhtar dayake ta tsilli-tsilli da ido, kana ta cigaba da faÉ—in "Shine na haihu sai waÉ—an nan suka kirani." ta nuna Na'ima da Raliya sannan ta cigaba "Shine suka ce suna son É—an in dai yadda shi zan yi, shine wannan ta bani kuÉ—i ta karÉ“e sa." ta karasa maganar da nuna Na'ima. Bappa ya dubi Dr Mukhtar ya sunkuyar da kai kasa yace "Abun da ta faÉ—a haka ne shin a asibitin ka akayi haka?." Dr Mukhtar ya shafa gefen fuskar sa daya kunbura in da bakwaren ya ya mare sa da adda, ya gyaÉ—a kai tare da faÉ—in "Eh haka ne a asibiti na ta haihu kuma ni na karÉ“i haihuwar, kuma wannan shine É—an." ya nuna É—an dake rike hannun Na'ima. salati kowa ya sake cike da É—inbin mamaki, masu tafa hannu suna tafa wa masu salati suna yi. Abbu ya dubi Na'ima yace "Mika musu É—an su." jiki a sanyaye cike da taren jin kunya ta tura musu É—an. bakwaren ya ja hannun É—an yana faÉ—in "Taho nine nan uban ka, ke kuma wuce muje ko na tsastsaga ki anan." ya kaÉ—a keyar yarin yar suka fita, yaja Æ´an uwan sa Æ´an sara suka yi gaba. Dr Mukhtar ma yaja kafa ya fita tsimi-tsimi Raliya ta bi bayan sa... Baya Ya SALEEM yayi yayin da hannunsa ke dafe da kirjin sa. a hankali ya shige cikin É—akin Ya Masa'ud. Mamie ta dubi Na'ima da take jin wani irin tsanar ta rai É“ace tace "Shi yasa ko dai-dai da rana É—aya ban taÉ“a jin son É—an nan ba ashe sabo da É—an shege ne ba jinina bane." Mamie ta juya ta nufi side É—in ta rai É“ace. shewa Aunty Rafee'at tayi tashiga tafa hannu, ta zo gaba Na'ima tana yi mata wani irin kallon sama da kasa tace "Ai dama karshen muna fuki jin kunya, duk wanda yace ruwan wani bazai tausa ba nasa ko lum-lum bazai yi ba, zakaran da Allah ya nufa da cara kuwa ko ana ga muzuro ga shawo sai ya yi, wacce kika lankaya wa tayi ciki da auren ta kika kazan ta mata ciki, gata a gaban ki ta zame miki abun kallon abin kwatance, É—an shege zaki kawo mana cikin family bama bukatan bare a cikin mu, fita mana agida makira algunguma kaÉ—an kika fara gani, sai duniya tayi juyin masa da ke." Aunty Jaleela tace "Kamar yanzu kuwa zaki fara ganin aya, sai kin gwammaci mutuwa da rayuwar ki, fita a kace fita mana agida." suka kaÉ—a ta har waje. niko ina taaye ina kallon abin kamar a Film, Bappa ya girgiza kai yace "Duk wan da ya nufi wani da sharri a kwan a tashi kan sa yake koma wa, Allah ka tsare mana imanin mu." aka amsa da amin kana muka juya muka koma ciki. kowa yana jinjina lamarin. har muka zazzauna ana alhenin abun. Bappa yana É—ago kansa idanunsa sukayi arba da wasu hotunan Inna guda biyu acikin glass É—aya, dake like jikin garun parlour'n, huf ya mike tare da nuna hoton da yatsa yana tafiya in da yake, cikin rawar murya Bappa yace "Adda A'i." da mamaki kowa ke kallon sa su Abbu suka mimmike tsaye, ya juyo da sauri yana faÉ—in "Wannan hoton a ina kuka samu?." Abba suka haÉ—a baki wajen cewa "Innar mu ce ka santa ne?." da sauri Bappa ya fita gurin mota yaje ya buÉ—e kana yabuÉ—e jakarsa dake cikin motar ya ciro wani hoto kana ya dawo cikin parlour da sauri, ya mika musu hoton wan da yake iri É—aya da É—aya daga cikin hotunan, da mamaki su Abbu suke kallon hoton iri É—aya da wan da yake jikin garun parlour, Bappa yace "Dai-dai da rana É—aya ban taÉ“a ajiye hoton a wani guri daban ba ko da yaushe yana cikin jakata sabo da girma da matsayin wacce take cikin hoton a guri na, Adda ta ce ita ta sha nono ta bar min, lokacin da Bappan mu ya rasu ina É—an kara mi, sai Æ´an uwan Baban mu suka É—auke ni suka tafini, kasanceaar ni na miji ne, suka barwa Maman mu Adda A'i, kamar yadda kuka sani mu fulani bamu fiye zama guri guda ba, musamman fulani makiyaya, haka mukayi ta yin nesa da in da mamar mu take,har muka sallaka Nigeria, tun da aka tafi da ni bansake haÉ—uwa da Maman mu da Adda A'i ba, bayan wasu shekaru masu dama aka zo ma na da sakon rasuwan maman mu da kuma wannan hoton, aka bani duk da lokacin da muka rabu da ita ina yaro ne sosai amma bai hanani gane Æ´ar uwa ta ba, lokacin da girma ya same ni na dawo Nigeria da kaina ban san kowa ba hansan ta inda zan fara neman Æ´ar'uwa ta ba, rugar mu da na rike sunan sa nayi ta bincike a kansa har naje rugar, duk wanda na tambaya sai ya cemin baima santa ba, a haka na fauwalawa Allah komai nacigaba da addu'a Allah ya haÉ—u mu da ita, haka na rika ajiyar hoton nan harrrana mai kamar tayau, ashe dai da rabon mugana ina Adda A'i take tana ina?." Abbu yace "Allah yayi mata rasuwa." salati Bappa yayi sai ga hawaye a idon sa, kowa sai da yayi kuka tuno da Inna..........! 8/19/22, 10:58 - Ummi Tandama😇: 32 Ummi ta rika bubbuga baya na tana faÉ—in nayi hakuri, yayin da hawaye ke cigaba da zuba a idanunta. da sauri na saki Ummi na juyo hawaye na zuba a ido na, na saki murmushi hawaye na zuba cikin matukar farin cikin ganin yau gani ga mahaifiya ta, na dubi Ahmad nace "My ga Ummi yau gani ga Ummi na, Bappa Ummi na ne Ummi na ne." sai na kuma rungumar ta ina hawaye haÉ—e da murmushi. wani irin farin ciki ne ya lulluÉ“e zuciyoyin su Ahmad yace "Barka da zuwa Ummi hakika mun yi farin ciki da zuwan ki." Bappa ko Masha alhmdllh alhmdllh yake ta faÉ—a yayin da fuskarsa ke bayyana jin daÉ—i. security kuwa gaba É—ayan su kowa yayi zuruu. Ummi ta share hawaye da gefen mayafin ta tace "Duk da sun kore ni na ayyana a raina bazan yi nisa da nan ba sai na ga HAMDAH da take cikin gidan nan dan jiki na na bani kece kiyi hakuri HAMDAH." na sake ta tare da faÉ—in "Ummi kiyi hakuri." sai kuma na juyo in da security suke nace "Uwa ta kuka yi wa wulakanci kuka hana ta shiga gidan duniya bana kiyama ba." Ahmad ya É—aga murya cikin tsawa yake ce da su, "A wani dalilin zaku hata ta shiga bayan ta sanar da ku ko wacw ce ita!?." suka haÉ—a baki wajen cewa "I'm sorry sir sabo da ba'a sanar mana da zuwan nata bane, kuma bayi zaton mamar Madam bace da gaske mun É—auka waÉ—an da suke alakanta kansu da ita ne kawai dan a barsu su shiga." Ahmad yace "Sai kuma baza ku iya kira ko zuwa ku sanar a kwai bako a waje ko ansan da zuwan sa ba? wani irin banzar aiki kuke ne!, an ajiye ku kurika wulakanta mutane ne a bakin get." Bappa yace "Sam bai dace ba ya kama ta idan irin haka ta faru, har idan ba'a sanar muku da zuwan bako ba, to idan yazo ba ku kore sa ba, ku nimi masaniya kan cewa an san da zuwan nasa ne sabo da wata rana zaku iya korin É—an gidan abun kuma ba zai yi kyau ba, to ba gashi yanzu kunyi a kan uwar mai gidan ba." Ummi tayi murmushi cike da Dattaku tace "A'a babu komai wlh, ai abakin ai kin su suke, kuma hakanne zai nuna tabbacin jajircewa kan aikin nasu, basu yi laifi ba sai dai kawai a kiyaye gaba." security suka shiga bawa Ummi hakuri kamar zasu zuba goiwowin su kasa, tace wlh har cikin ranta babu komai kuma bataji haushi ba dan a bakin ai kin su suke. na ja hannun Ummi cikin farin ciki muka yi ciki in da na karÉ“i jakarta na rike a É—aya hannuna. da sauri Inna Wuro ta fito dan Faty taje ta sanar mata Ummi na ta zo, a tare duk muka É—unguma mukayi cikin parlour, Bappa yace shi zai shiga Masallaci bari su yi salla zai shigo su gaisa, a parlour Ahmad ya mika min Ahmad karami yace shima bari ya je yayi salla. gaba É—aya baki na yaki rufuwa farin cikin da nake jin kaina ciki tamkar anyi min albashir da aljanna. a kan kafar Ummi na dire Ahmad karami, Ummi ta rike sa ta na faÉ—in "Yaya sunan sa?." nace Ahmad. tace Masha Allah Allah ya raya da imani." su Talatu suka shigo parlour'n suna kwasar gaisuwa da tayani farin cikin zuwan Ummi na. Ummi ta kurawa Naseem da Nasmah ido da suke ta tsalle gefen ta sunayi wa Ahmad karami kawa, ta dube su da murmushi tace "Yaya sunan ku?." kusa da ni Naseem ya zo ya kawo bakin sa kunne na yace "Mommy ita yaya sunan ta." ido na waro tare da saurin toshe kunne na wai shi a dole magana a hankali zai yi kada kowa yaji amma kamar ihu yayi min cikin kunne. dariya duka parlour'n a É—auka, nace "Mama na ne fa kun gaishe ta kuwa, sunan ta Ummi." murmushi Ummi tayi yayin da ta kasa janye idanunta kan yaran, ta janyo hannunsu tana faÉ—in "Bari na faÉ—a muku sunana kuma sai ku faÉ—a min naku, suna na Ummi ku ya sunan ku?." Naseem ya washe baki yace sunan sa Naseem ita kuma sunan ta Nasmah. ai ko Nasmah ta shiga bubbuga kafa kasa wai ita zata faÉ—i sunan ta da kanta. Ummi tace "To faÉ—a min naji ban ji nashi ba." ta washe baki tace Nasmah. ai ko surutun su suka shiga cike ta da shi, suka rika bata rabaran da bata san tushin sa ba, har da labarin gobe Dadday'n su yace zai É—auke su da kanin su ya kai su ya kara siyo musu lilon doki. Nasmah ta wawwaro ido tace "Kuma muna da wani har guda haka kuma Daddy'n mu yace zai kara mana guda haka." tayi mata nuni da yatsun ta huÉ—u da kuma biyu wan da za'a kara musu. Naseem yace "Zo kiga lilon dokin mu yana kusa da É—akin É—awisu ne fa." yayi maganar shima yana wawwaro idanu Ummi tace "To sai gobe zan je na gani." Nan da nan nasa su Zulai suka cike ta da kayan ci da sha.. Su Bappa da Ahmad suka shigo su ka zauna bayan sun gaisa da Ummi akayi ta hira. gaba É—aya nakasa zaune na kasa tsaye farin cikin ganin Ummi na yasa bakina ya kasa rufuwa farin ciki na yagaza É“uya, ina jikin Ummi na naki matsawa ko nan da can, a É“angaren Ummi ma haka abun yake farin cikin da take jin kanta ciki yau bazai misaltuba, sai kallon É—iyar tata take, yan da ta kara girma ta zamo cikakkiyar mace, ga Æ´aÆ´an da take ganin su a gaban ta wai duka Æ´aÆ´an HAMDAH ce, Allah mai iko buwayi gagara misali. Bappa ya mike yace a barta ta huta ya fita, Inna Wuro Faty Talatu Zulai duk suka yi mana sai da safe suka tafi. cike da girmamawa Ahmad ya mike ya lura Ummi nauyi take ji yasa ta kasa cin komai a gaban su, ya dubi su Nasmah yana faÉ—in "Naseem Nasmah kuzo muje mu bar Ummi ta huta." ya ja su suka haura sama. nace "Ummi muje sama kiyi wanka kici abinci ki huta." tace "A'a nan ma ya ishe ni ba sai na haura ba." murmushi nayi dan nasan ganin Ahmad ya haura ne, na mike na É—au jakarta nace "To ki shigo nan Ummi." nayi maganar ina nufar É—aya daga cikin bedroom É—in cikin parlour'n. ta biyo bayana rike da Ahmad karami da yayi bacci, É—akin a gyare yake tsaf dan kullum sai su Talatu sun gyara É—akunan duka. Ummi ta rika bin cinin É—akin da kallo kana ta shinfiÉ—a Ahmad kan gado ta shige bathroom ni kuma na fito parlour, abincin da aka kawo mata bata ci ba na kwashe na kai mata É—akin, ina zaune ta fito tayi wanka haÉ—e da al'wala, na shinfiÉ—a mata sallaya, ta gabatar da salla. tana idarwa na zuba mata abinci tana ci muna hira sai da naga taci abincin sosai kafin na mike nafita. na haura sama na tadda tuni su Naseem sunyi bacci Ahmad yana kwance a gefen su. yana gani na ya mike ya janyo ni jikin sa, goshi na ya sumbata kana ya É—ago da murmushi yace "An ga Ummi shine za'a mai da ni marayan gasken-gaske ko?." dariya nayi tare da jan É—an karamin gyamun sa nace "Maraya kuma kana da ni da Aunty Rasheedat kake kiran kanka maraya." hannunsa ya sakalo ta kugu na ya daÉ—a haÉ—e jikin sa da nawa kana yace "To a sallame ni dan yau nasan ba lallai naji É—umin jikin kiba." murmushi nayi nace "Ai kuwa kamar ka sani gurin Ummi zan kwana." yace "Na sani ai kuma na yafe dan nasan a yanzu Ummi ta fini bukatar ganin ki kusa da ita,amma fa zan yi fama sosai na rashin ki kusa da ni." nace "Kaje guje gurin Aunty Rasheedat mana nima bana so na barka kai kaÉ—ai." yace "A'a ai da ni za'ayi murnar ganin Ummi'n nan." yayi maganar yana jan kumatu na. dariya nayi kana a sannu na kai lip's É—i na ka nashi, sai da na ai ka masa da kwararan sakwanni na wan da nasan zai sami bacci cikin nutsuwa kafin na zame jikina na koma gun Ummi... Ina shiga na tadda tana waya tana faÉ—in "Yanzu haka ma ina cikin gidan a É—aki ina shirin kwanciya Yaya." na karaso ciki da sauri tun da naji tace Yaya yasan Abbu ne take wayan da shi. daga cikin wayar cikin matukar farin ciki Abbu yace "Ina HAMDAH ina HAMDAH take?." Ummi da bakin ta ya kasa rufuwa tace "Ga ta nan bari na bata." ta mika min wayar tana faÉ—in "Abbu'n ku ne." a gefen ta na zauna tare da kara wayar a kunne nayi sallama, Abbu ya amsa yana faÉ—in "HAMDAH HAMDAH kece?." wasu zafafan hawaye ne naji sun zubo min a hankali naji saukar hannun Ummi kan fuska ta tana share min, sai na saki murmushi mai sauti nace "Ni ce Abbu ina yini." Abbu yace "Alhmdllh ita ce." hele najiyo daga cikin wayar da hayaniya idanuna na lumshe nakuma buÉ—e wa jin muryoyon Æ´an uwa na, Abbu yace "Masha Allah alhmdllh sannu sannu HAMDAH sai mun zo maganar waya bazata wadatar da mu ba." muryar Aunty Rafee'at najiyo tana faÉ—in "Abbu bani inji muryar ta." tace "HAMDAH." nace "Na'am Aunty Rafee'at." sai kawai ta fashe da kuka, nima kukan na fashe da shi. Abbu ya karÉ“i wayar yana faÉ—in "To yanzu kam hankali na daf da kwanciya Rafee'at Jaleela kowa ya tafi gida sai kuma ranar tafi." cikin shessheka Aunty Rafee'at tace "Abbu Ina gobe ne zamu tafi." yace "A'a sai jibi kuje gobe a shirya jibi a tafi." farin cikin da na tsinci kai na ciki bazai misaltuba jin muryoyin Æ´an uwa na. Abbu ya kashe wayar, Ummi ta rika rarrashi na ganin naci gaba da kukan har sai da taga na daina kukan. ranar kusan kwana mukayi muna hira da Ummi... washegari da kaina na shiga kitchen muka shirya abun breakfast iri-iri, na kwashi na Ummi na kai mata cikin bedroom É—in da take, na É—au na Ahmad na kai masa sama, sai da na tayasa wanka kafin ya barni na sauko. ni dai a É—akin Ummi nayi wanka dan na sauko da kayan da zan sa da na Ahmad karami, Ummi da kanta tayi masa wanka ta shirya shi. su Naseem ne suka shigo da shirin tafiya school Ahmad na biye da su, cike da girmamawa ya tsunkuya ya gaida Ummi da tambayar ta gajiyar hanya, ta amsa fuska a sake. nan ma Ummi tayi ta kallon yaran har suka fita, tabbas yaran suna mata mugun kama da SALEEM musamman Naseem yafi kama da shi sosai, a ranta take faÉ—in ko dai sune cikin da ta tafi da shi, sai kuma ta kakkaÉ“e zuciyar ta da wannan tunanin, bayan ga ubansu nan tana gani, ai dama HAMDAH kama suke da SALEEM dan Æ´aÆ´an ta sun yi kama da shi ba abun mamaki bane. na lura da kallon da Unmi take ta yiwa su Nasmah, nasan tarin bambayoyi ne tare da ita musamman kan yaran, sai dai har yanzu bamuyi wannan hirar da ita ba. bayan munyi breakfast tare da Ummi, muka fito parlour. Inna Wuro ta shigo, dan yanzu bata kwana cikin side É—in nan tun da mukayi bakwai sai dai da safe ta shigo tayiwa Ahmad karami wanka,da yamma ma haka. bayan sun gaisa da Ummi nima na gaishe ta, nace "Inna Wuro shine yau baki zo kinyiwa Ahmad wanka ba." dariya tayi tace "Ai ni yanzu na sake wa matar sa tayi masa wankan arba'in É—in." hire sasoi muka yi ta yi, ina like kusa da Ummi na, a ranar da yamma Aunty Rasheedat ta zo yiwa Ummi barka da zuwa, bata bar gidan ba sai dare suka koma da Ahmad. Ummi ta yaba da halinta kwarai da gaske tayi ta mamaki da na ce mata matar Ahmad ce.... Kamar yadda Abbu yace bayan kwana biyu da zuwan Ummi suma suka É—au hanyar zuwa Abuja, koda suka iso Ummi ta haÉ—a mu da su a waya nayi ta musu kwance har suka iso. koda suka iso suka ce gasu a bakin get nan da nan nasa security suka buÉ—e musu get, ina jin shigowar su da sauri na fito, motoci biyu suka taho da shi na Abba da Abbu. Aunty Rafee'at ne ta fara fitowa daga cikin mota, wani irin kallo muke bin junan mu da shi, Aunty Rafee'at kuwa kallon yan da na kara girma da cika take, da gudu ta taho nima nasa gudu muka rungume juna. Aunty Jaleela Ya Masa'ud Nusaiba Fauzan Mamie Abbu Abba duk suka fito, sai na saki Aunty Rafee'at nayi gurun su, yan da na shiga rungume su sai ya tuna min da lokacin da suke zuwa Dass gurin Inna haka zanyi ta rungume su ina yi musu oyoyo, sai kawai na fashe da kukan farin ciki, duk kanin su sai da suka yi kwalla. jiki a sanyaye na matso in da Abba yake tsaye, yana duba na cike da nadama a gaban sa na tsaya ban iya rungume shi. sai ya miko min hannu alamar na zo, jiki a sanyaye na maso in da yake, kai na yashafa tare da bubbuga kafaÉ—a ta. kai na sunkuyar jin hawaye ya ciko min ido sai ga hawaye sharr. Mamie ta matso in da nake ta janyo hannu na tare da girgiza min kai, Ya Masa'ud ya leko fuska ta yace "Kai Æ´ar gidan Inna har kin fi Jaleela girma yanzu." dariya nayi hawayen na zuba. Aunty Jaleela kuwa harararsa tayi tana murmushi, ciki duka mukayi har da su Bappa da suka fito, muna shigs na kira Ahmad na sanar masa isowar su batare da É“ata lokaci ba suka iso shi da Aunty Rasheedat... cike da sha'awa su Aunty Rafee'at suka yi ta É—aukar su Naseem da suke ta zuba musu surutu. Mamie ko ido ta rika binsu da shi lokacin da ta janyo su jikin ta, Naseem ta yi ta kallo ganin suffofin SALEEM lokacin yana karami tare da shi... Su Abbu sun sha mamakin ganin Ahmad Sabil sun jinjina lamarin da ganin tabbas da gaske shi miji na ne.... Bayan gaishe-gashe daya gaba ta, cin abinci ya biyo baya, daga nan kuma sallar la'asar aka tashi yi, in da su Abbu suka tafi masallaci, su Mamie kuma suka shiga É—akunan da suke cikin parlour'n kasa sukayi salla. bayan anyi sallar aka kuma dawowa parlour. bayan an zazzauna Bappa yayi gyaran murya ya soma magana...........! Kuyi mane ji ina da ba'ki yau idan Allah ya kaimu gobe na sami lokaci zan kara muku👌 wlh yanzu ma da kyar na samu nayi wannan É—in 8/19/22, 10:58 - Ummi Tandama😇: 35 Bayan wani lokaci.. ranar wata laraba zaune nake a parlour'n kasa, najiyo sallamar hajiya Karima. na amsa tare dayi mata barka da zuwa, ta amsa tana zama kan kujera, wasa ta shiga yiwa Ahmad karami da ke zaune a kasa kan carpet rike da pida a hannunsa yana shan madara. na gaishe ta ta amsa fuska sake tana tabbaya ta ya kwanan gidan da yaran. nace kowa lafaya. ta dube ni da kyau tare da gyara zaman ta tace "HAMDAH nazo ne dama na nimi gafarar ki da kuma sulhu, hakika nasan abin da na ai kata a baya ban kyauta ba, na gane kuskure na Ahmad É—ana ne, kullum cikin ladabi da biyayya yake agare ni, me zai sa naso ganin bayan sa, i naso ki rufa min asiri kada ki faÉ—a masa komai, duk da nasan ko da kin faÉ—a masan ma bayar da zaiyi ba, sabo da irin ki sun sha faÉ—a masa baya yarda, ina so na gyara kuskure na shi yasa nazo na sanar miki yanzu duk na zubda makamai na, me zai sa na so kashe Ahmad wanda yaÉ—au keni matsayin uwa, sharrin shaiÉ—an ne, yanzu zuciya ta É—aya yake, kuma zan same sa cikin dabara na nimi gafarar sa." É—an shiru nayi ina duban ta yan da take maganar gaba É—aya yanuna zallar gaskiyar ta take faÉ—a, kai na jinjina kana nace "Babu komai hajiya Allah ya tsare mu da sharrin shaiÉ—an." na mike ina mai jin daÉ—in maganar ta ina ayyanawa a raina yanzu zan zo na kira Ahmad na sanar masa, Hajiya ta yada makaman ta, nasan shima yanzu zuciyar sa zata sami salama. na tufi kitchen domin na samo mata É—an abin taÉ“awa, matar nan tana bani mamaki idan ka ganta tamkar mutumiyar kwarai amma zuciyar ta baki, gara da yanzu Allah ya ganar da ita tana da rabo... kayan ci da sha na shirya su a kan tray kana na É—auka na nufi kofa. da sauri nakarasa fita daga cikin kitchen É—in jin ana tafa hannu, turus na naja na tsaya nan bakin kofar kitchen ganin Ahmad tsaye cikin parlour'n yana tafa hannu tare da dumfaro Hajiya Karima dake rike da Ahmad karami ta kawo fida daf bakin sa tana kokarin saka masa shi cikin baki, cak ta saida hannunta bata sauke hannun ba bata kuma kara sa dashi cikin bakin nasa ba, yayin da hannu yake rawa. ya karaso gaban ta yana mai cigaba da tafa hannu ya dube da kyau tare da faÉ—in "Da kyau Hajiya ya kika da kata kuma bashi ya sha mana." da sauri na karaso in da suke na dire tray É—in saman table nace "My Hajiya ta gane gaskiya tace yanzu babu komai cikin ranta." "Shiru HAMDAH." yayi maganar tare da É—aura yatsar sa kan lips É—in sa, kana ya dubi Hajiya Karima da gaba É—aya ilahirin jikin ta ke É“ari sai ta shiga kame-kame tana faÉ—in "Ah..la... Ahmad..kuka yake shine na É—auke sa na bashi madarar sa, da na gani a nan." hannayen sa ya naÉ—e a kirki yayin da idanunsa ke kan ta yace "To sha fara sha kafin kiba shi ya sha, sha yanzu!!!." yayi maganar cikin tsawa sosai, daga ni har ita sai da mukayi wani irin zabura. yadube ni kana ya soma magana cikin fusatacciyar murya sosai. "Duk abun da ta faÉ—a miki yauda ra ce bazata taÉ“a sauyawa ba." kana ya mai da duban sa kan ta yace "Kin jima kina cutar dani, kin yi sanadiyar rasa mahaifa na,ni kaina kina bibiyar rayuwa ta, hakan baiyi miki ba har da É—ana cikin jadawalin ki! to ki sani rayuwa ta dana É—ana ba a hannunki yake ba ke baki isa kiyi mana abinda Allah bai hukunta ba, mutuwar mu ba a hannunki yake ba, basai kin kashe mu ba ki jira idan lokacin mu yayi zamu tafi dole ba makawa, me wannan jaririn ya tsare miki da zaki zuba masa guba cikin abin shan sa, muddin ina numfashi bazaki taÉ“a kuma cin galaba kan ahalina ba!!, duk wani motsin ki a tafin hannuna kike yin sa, lokaci na É—ebar miki, domin hukun taki kan abun da kika jima kina ai kata shi, kuma lokacin yayi dan haka." wani irin razana nayi da sauri na sunkuci Ahmad karami dake ta raba ido kan kafarta, na rungume shi ina duban bakin sa ko har ta bashi madarar. kofa ya kalla tare da faÉ—in "Kushigo." da mamaki na maida duba na kan kafor, wasu mutane ne guda huÉ—u suka shigo, yace "Kutafi da ita." suka dube ta suna faÉ—in "Oya mike." duk wani roko da magiyar da take wa Ahmad bai saurare ta ba yace a tafi da ita, suka saka mata ankwa sukayi gaba da ita... Numfashi na sauke tare da duban Ahmad da ya zube kan kujera tare da shafa kansa. jiki a sanyaye na zauna kusa da shi, na dube shi jiki a sanyaye nace "My na É—auka da gaske Hajiya ta tuba da bakin ta take faÉ—a min É—azu har tace zata nimi gafarar ka." shafo gefen fuska ta yayi, yace "Kyakkyawa ta ai tayi hakan ne dan ki yarda da ita har ta cimma burin ta, Hajiya bazata taÉ“a sauyawa ba sabo da son duniya ya rigada ya gama rufe mata ido, kuma abun da bata sani ba sam bazata taÉ“a zamo silar rasa rayuwa ta dana É—ana ba, idan tayi hakuri ma zan tafi na bar mata duniyar dan ba mai tabbata a duniyar nan." ya mika hannu ya karÉ“i Ahmad karami dake ta zame wa yana son zuwa gurin sa, É—an kwanciya nayi a gefen jikin sa ina mai jin son sa da tausayin sa yana shiga na, É—an É—ago kaina nayi ina duban fuskar sa kana nace, "My wai ya akayi ne kake san duk shirin ta, ya akayi ne ma kasan ta zuba guba cikin abun shan Ahmad?." murmushi yayi tare da sumbatar goshin Ahmad karami, kana ya É—an karkato ya ja kumatu na sannan yace "Ai ki na ne fa a kan wasu bare kuma ni kai na, jami'in sirri." da mamaki na ke duban sa cikin kuma rashin fahimta nace "Jami'in sirri?." kai ya gyaÉ—a yana murmushi tare da ruko hannuna yace "Eh ni SS ne kece mutum na huÉ—u da kukan koni waye Daddy na da Mommy na da kuma Kawa." cikin matukar mamaki nake duban sa, ban taÉ“a zato ko sammani ba, ban taÉ“a ganin wata alama a tare da shi ba, lallai kuwa waÉ—an nan jami'an sun san ai kin su, in ba wai sun so ka san ko su waye bane ko shekara dubu zakayi da su baza ka taÉ“a sani ba, tunanin hirar da Bappa ya taÉ“a min akan sa na lokacin da yaje rugar su ya kama É—aya da gacikin makiyayin su, wan da basu san cewa shi É—an fashi bane, ashe dai dama aikin sa ce ya kai shi can. maganar sa ce ta katse min tunanin da nake "Kiyi min alkawarin ko bayan raina Ahmad zai gaje ni." da sauri na dube shi jin abin da ya faÉ—a mai haÉ—e da kalmar ko bayan ransa. murmushi ya yi tare da kawar da maganar da wata zancen da ban..... *Bayan wata biyar* Zaune muke a parlour dukan mu cike da walwala da jin daÉ—i, sai dai tun waye war garin yau na sinci kaina cikin matsanan ciyar faÉ—uwar gaba da son yin kuka. haka nayi ta daure wa ina ta son gusar da fargabar da bansan dalilin yin sa ba. Ahmad karami da yanzu yafara tafiya sai gujegujen su suke a sakiyar parlour shi da su Naseem, ina kwance jikin Ahmad sai binsu da dariya muke cike da shauki. É—an muskutawa nayi na É—ago kaina ina duban fuskar sa nace "My last month É—in nan zan yaye yaron nan." yace "A'a kam gaskiya ba yanzu ba ki bari ya kara wata biyar nan gaba sai a yaye shi." ido na waro nace "Cap wata biyar wannan katon yaron da kowa yagan sa yake cewa har yanzu ban yaye shi ba, wani irin girma kake so yayi kafin a yaye shi, ni dai Allah ya ishe ni da tsotso." "To masu faÉ—an ai basu san watannin sa bane dun sun gansa da girman jiki wannan É—an jaririn suke cewa a yaye shi, wani shan nono ma yake yaron da zai wuni yana wasan sa bai zo in da kike ba." baki na turo tare da bubbuga kafafuna kan kujera nace "Ni dai kam watan nan na kare wa zan kai wa Aunty Rasheedat shi ta yaye shi." yace "To ya isa ba sai anyi min rigima ba zan yi tunani amma dai kafin nan taso muje kiji wani magana." kafaÉ—a na make ina dariya nace "A'a faÉ—a a nan basai mun shiga ciki ba naki wayon, ina dai yanzu muka fito." a hankali ya raÉ—a min "Kari zanyi." dariya nayi ina make kafaÉ—a.. wayar sa ce tayi kara ya É—aga. bayan yagama magana ya sauke wayar kana ya dube ni da murmushi yana faÉ—in "Alhamdulillah wasu kuÉ—aÉ—en da Daddy ya bada kwangilar wasu kamfanoni guda uku kafin ya rasu, ba a fara aikin ba ya rasu sai a ka dakatar da aikin, waÉ—an da a ka basu kuÉ—in basu dawo da shi ba sai yau, lauyan sa ne ya kirani yanzu nazo na karÉ“i kuÉ—in." mike wa zaune nayi ina faÉ—in "Masha Allah an godewa Allah." ya mike yana faÉ—in "Bari naje yanzu wai ni a ke jira." nace "To a dawo lafiya." har yakai bakin kofa ya jiyo ya kuma dawowa cikin parlour'n, in da su Naseem suke ya isa ya sunkuya dai-dai tsawon su, ya shafa kan ko wannen su yace "Allah yayi muku albarka kuyi rayuwa mai kyau da inganci, kowa ya bani sallamar sa anan fita zanyi." yanuna musu gefe da gefen kumatun sa. cikin washe baki Nasmah ta sumbaci gefen kumatun sa na dama Naseem kuma É—aya gefen, ganin abun da suka yi Ahmad karami shima ya maso ai kuwa ya yanka masa cizo a kuma tu. dariya dukkan mu muka yi, kumatun ya shafa yana faÉ—in "Ash Ahmad sallamar taka kenan?." karaso wa in da suke nayi ina dariya nace "Oh Ahmad haka aka ce maka suka yi ne." yaÉ—a ga shi sama ya na juyi da shi sai washe baki yake, daga bisani ya dire shi kasa. yayi ta biye wa yaran suna ta wasa sai da nace masa, ya tafi ko ya mance a na jiran sa. nan ma har ya kai kofa yakuma juyowa, ya kira yaran tare da buÉ—e hannayen sa suka so da gudu ya haÉ—a su duka ya rungume su. ido na É—an kura musu yayin da fargaba mai haÉ—e da faÉ—uwar gaban nan ke daÉ—a taso min. maganar sa naji yasani saurin mai da hawayen da naji suna kokarin zubo min. "Zo mana kyakkyawa ta." yafaÉ—a yana min alamar nazo kusa da shi, jiki a sanyaye na taka zuwa in da suke, sai ya janyo ni duk ya haÉ—a ya rungume mu, a tare muka sauke ajiyar zuciya ni da shi. duk kanin mu shiru mukayi muna cikin jikin sa, yayin da zuciya ta ke wani irin bugawa. jin yanayin nason firgita ni sai na É—an mosa, a hankali ya sake mu yana binmu da murmushi. da sauri na maso jikin sa na ruko hannunsa na kankame shi gam, murya na rawa tuni hawaye yafara zubo min nace "My tsoro nake ji." Naseem da Nasmah ya kalla yace "Kuje kasa kujira ni gani zuwa yanzu." suka amsa da sauri suka nufi parkour'n kasa, da sauri ya janyo ni ya rungume ni tare da haÉ—e bakin mu, da karfe na daÉ—a rungume shi ina daÉ—a cusa baki na cikin nashi. yayin da nake jin numfashi na ke yin sama-sama, da sauri na janye bakina sai kawai na saki kuka ina jujjuya kaina. da sauri ya rirrike ni cikin muryar dariya yake faÉ—in "Ke lafiyar ki kyakkyawa ta meye kuma na kukan kuka baya baki wuya ke, to ya isa faÉ—a min me ya saki kukan." baki na turo ina jan shesshe ka. "Mene ne me ya same ki?." kai na girgiza dan nima ban san dalilin kukan nawa ba. hawayen yashiga share min yana faÉ—in "To bana son wannan kukan ko nan gaba dan Allah kiyi min alkawarin zaki daure, addu'a yafi komai tasiri a kan koma me, aduk san da kika ji tsoro ko fargaba ko faÉ—uwar gaba ko wannan kukan kiyi kokarin danne su ta hanyar faÉ—in Innalillahi'wa'inna'ilaihirraji'un, wannan kalmar yana samar wa zuciya nutsuwa,shagwaÉ“aɓɓiya ta." ya karashe maganar cikin sigar zolaya tare da jan kumatu na. yaci gaba da faÉ—in "Ni bari naje kar su gaji da jira na, kiyi min shiri mai kyau anjima yau ina sa ran da zaran na jefa kwallo na ya isa raga, Ahmad nason kani ko kanwa." yayi maganar yana kashe min ido, baki na kuma turo wa cikin muryar shagwaÉ“a nace "Ka mance gun Aunty Rasheedat kake." kai ya dafe yace "Oh wlh gaba É—aya na mance amma dai zan dawo kafin dare ayi min shiri kawai." haka yayi ta jana da wasa da kuma salon zolayar sa mai sani nishaÉ—i har sai da yaga na ware har da dariya ta kafin ya sake ni, ya juya zai fita Ahmad karami dake wasa gefen mu ya saki wani irin kuka, yana mika masa hannu. da sauri ya dawo ya É—auke sa yashi rarrashin sa, sai da yayi shiru kafin ya mika min shi yana faÉ—in "Je ka gurin Mommy kada ka sake kuka, kada ki barshi ya sake yin kuka ki tsaya masa ya kasan ce cikin farin ciki, mu je ayi min rakiya ko." na bi bayan sa muka sauka kasa, nan muka tadda su Naseem duk mukayi waje tare. ko da muka isa parking lot ya karÉ“i Ahmad karami yayi ta masa wasa yana kyalkyale dariya su Nasmah ma haka, sai da ya gama yiwa yaran wasa kana ya mika min Ahmad yace bari yaje ya sanar wa Bappa Yakamata ya sami labarin da wuri. muna tsaye a parking space yaje ya dawo,yake sanar min Bappa ya taya sa murnar fitowar makudan kuÉ—a É—en sa. yashige mota muna É—aga wa juna hannu har ya fita, numfashi mai karfi na sauke san da motar sa ta É“ace wa gani na, jiki a sanyaye na juya muka koma ciki.... Da misalin karfi 6 da yanma, har zuwa wannan lokacin ina dai nan ne amma gaba É—aya yanayin baya min daÉ—i, kiran Ahmad ne ya shigo waya ta da sauri na É—aga tare da yin sallama. ya amsa yana faÉ—in "Kyakkyawa ta mun gama komai na karÉ“o kuÉ—in gasu a mota, sai dai banki yanzu sun tashi zan kai su gida gobe zan sa a kaisu banki." "Masha Allah mun gode wa Allah, amma My kai kaÉ—ai kake tafi babu security?." yace "Tare da su muke, ina zuwa." ya faÉ—a tare da É—an yin shiru, jin abun da yake faÉ—awa security yasani faÉ—in, "My mene ne?." yace "Wasu mota ne guda biyu suke bayan mu tun É—azu na lura kamar biyo mu suke, ina son sanin ko su waye ne." jin yana kokarin kashe wayar da sauri nace "My kada ka ci gaba da tafiya da su ku canza hanya ni dai hankali na bai kwanta ba kaji dan Allah." yace "To yan da kika ce haka za'ayi kyakkyawa ta." ina tsaye cikin É—aki rike da waya sai kaiwa da komo wa nake da kyar na samu na iya zama, tafiya da kuÉ—i masu yawa a mota irin haka a kwai hatsari sai dai saukin ma É—aya yana tare da jami'an tsaro. da sauri na É—aga waya shigo war kiran sa yace "Kyakkyawa ta na iso gida ta hanyar canza hanya kamar yadda kika faÉ—a." numfashi mai karfi na sauke nace "Kai alhmdllh amma wlh duk a tsorace nake har naji hankali na ya kwanta." yace "To je kiyi salla kiyi mana addu'ar dace wa da rahamar Allah nima masallaci zan tafi yanzu." nace to... Da misalin Æ™arfe goma na dare ina kwance sakiyar yara na yayin da waya ke kare a kunnena kamar kullum, a duk san da Ahmad baya gida na to muna tare da shi a waya, ko yanzu hira da shi muke ta waya. hamma nayi haÉ—e da mika tare da yin salati nace "My bacci." yace "To sai da safe kiyi baccin ki mai daÉ—i." murmushi mai sauti nayi nace "Kai ma haka." na kashe wayar,na bi yaran da addu'a nima na shafa na gyara kwanciya ta, wani irin faÉ—uwar gaba naji da sauri na dafe kirji na, a hankali na fara nanata kalmar Innalillahiwa'inna'ilaihirraji'un³. gaba É—aya bacci ya kairace a idona ina dai kwance shiru. can wajen karfe 2 na dare har lokacin ina kwance idanuna kuma biyu, da sauri na janyo waya ta dake tsuwa karkashin pillow, ganin mai kiran nawa yasa ni saurin mike wa zaune na kai wayan kunne na tare da faÉ—in "My." yace "Baki bacci ba kyakkyawa ta?." nace "Na kasa nakasa yi My." numfashi ya É—an sauke tare da faÉ—in "Ko na zo ne." kai na girgiza da sauri nace "A'a dare yayi sosai." yace "To ki tashi kije kiyi al'wala kiyi nafila ko da raka'a biyu ne kiyi addu'a zakiyi Baccin." nace to. yace "Ina su Naseem?." "Ga sunan suna bacci." "Shafa min kansu duka ki sakawa Ahmad wayar a kunne." nace "Yana bacci ai." yace "Eh sa masa." a hankali nayi yanda yace na saka masa wayar a kunnen sa, magana ya soma yi a hankali yace "Ahmad Ahmad Tijjani Sabil, kada ka bari wannan sunan ya mutu, kada ka sake duniya ta mance da wannan sunan duniya ta cigaba da faÉ—ar waÉ—an nan sunayen, kamar yadda nayi tsayuwar daka domin ci gaba da É—aukaka sunan Tijjani Sabil da har yau duniya basu mance da shi ba,suna kuma yi masa addu'a a koda yaushe, Allah ya dauwamar da albarka cikin rayuwar ka kai da Æ´an uwan ka." da sauri na É—ago wayar a kunnen sa ganin yana motsi, nace "My me kuma ya kawo wannan maganar a daren nan?." murmushi mai sauti yayi yace "Kiyi hakuri kyakkyawa ta." nace "Na me fa?." yace "Ba komai rayuwar ce dai dole sai da hakuri, Ahmad yana son ki da kaunar ki." numfashi na sauke zuwa yanzu maganganun sa na tun waye war garin yau da kuma yanzu sun fara da mi na, suna son su haÉ—e su cunkushe da yanayin fargaba da faÉ—uwar gaban da na ke ji. nace "My nima ina son ka da kaunar ka." yace "Nagode kyakkyawa ta, kin san me?." nace "Sai ka faÉ—a." yace "ÆŠazu ban zo da kuÉ—in nan gida ba a hanya na kira manajan banki yazo sai mukayi canjen mota na bashi nawa wan da kuÉ—in yake ciki na karÉ“i nashi, shi ya tafi da nawa gidan sa gobe zai shige da shi banki." nace "Ai ma hakan yafi gara da ka bashi kaga idan zai tafi ban kin sai ya tafi da shi yafi sauki ma." jin ya É—anyi shiru baiyi magana ba nace "My kai ma bacci kake ji ka kwanta sai da safe." yace "A'a naji karan buÉ—e get ne." nace "A cikin daren nan?." "Ai nima shine na gani bari naje na ga ko waye mai gadi ke buÉ—e wa get da daren nan ina zuwa." ya kashe wayar tare da duban qRasheedat dake kwance a gefen sa, ya mike ya sauko a gadon ya fito. a hankali yake tafi ya har ya fito, ga mamakin sa sai yaga an kakkashe wutan gefe da gefen gidan har zuwa lungunar dake cikin gidan duk wutan a karkashe, iya wutan dake can bakin get da kuma na hanyar shiga side É—in sa da na Rasheedat ne kawai a kunne. can ya hangi security kwakkwance a gurin zaman su duk suna bacci ko wannen su ya yada bindigan shi gefe suna ta sharar bacci. gefe can kuma karnukan gadi ne suna zazzaune sai fidda harshe da ciccire ido suke. motsi yaji a ta gefen sa in da babu hasken wuta a gurin, a hankali ya mai da duban sa gurin ya kurawa gurin ido sosai, inuwar mutum ya hango tsaye a gurin. da sauri ya waiga É—aya gefen sa nan ma yakuma hango inuwar mutum, a hankali yayi baya yarika tafiya da baya da baya cikin hanzari ya koma ciki, da sauri ya shige bedroom É—in sa, ya isa jikin gado ya saka hannu sa kasan gado yaja sai ga drower ya bayyana yaciro bindiga ciki ya mai da drower ya É—ago yana gyara rukon bindigan a hannunsa. Rasheedat ce tayi juyi tare da ware idanun ta a kansa, da sauri ta mike zaune tana faÉ—in "Aboki lafiya?." yace "Æarayi sun shigo gidan nan." ido ta waro da sauri ta duro a gadon tana faÉ—in "Ina security suke har É“arayi suka sami damar shigowa gidan nan?." yace "Akwai matsala suna nan abin mamaki duk kanin su bacci suke." ya juya da sauri yana kokarin fita tasha gaban sa da sauri tace "Aboki ina kuma zaka je?, a'a kada ka fita, kayi waya wasu jami'an suzo, kasan da abin da suka zo, hakika da abin da suka taka tun da har kaga suka iya samin karfin guiwar shigo wa gidan nan duk tulin tsaron da ke gidan nan." yace "Nasan abun da ya kawo su kuÉ—in nan ne kuma baya gidan nan ma zan je naji da su." ya juya da sauri. da gudu ta bi bayan sa ta rungume shi ta baya tana faÉ—in "Aboki kada ka fita ka tsaya na buÉ—e maka kofar baya ka fita ta can dan Allah kada kaje." juyo wa yayi ya rungume ta yace "Kawa ki zauna duk abunda zakiji kada ki fito, kiyi min addu'a kinji." kai ta shiga girgiza wa tare da sakin kuka tana faÉ—in "Aboki kada ka je na roke ka ka fita ta kofar baya." jikin sa ya zare daga nata, lokacin da aka fara harbi cikin gidan, ya tallafo fuskarta yace "Kiyi min alkawarin ba zaki fito ba duk abun da kika ji, kizauna cikin É—akin nan ki kulle kanki bazan taÉ“a barin su sushigo ciki ba zan kare ki da yardar Allah,sannan kuma bulet bazai iya É“ula ginin gidan nan ba ko da ace sun yi yunkurin yin harbi cikin nan, kada ki fita kizauna a nan." harbi aka cigaba dayi cikin gidan ta ko ta ina, Rasheedat ta daÉ—a kankame shi tana faÉ—in kada ya fita. da sauri ya sake ta ya fita. ita ko kuka ta kuma sake wa ta durkushe a gurin, sai kuma ta mike da sauri ta isa ta kulle kofar, ta koma bakin gado tana cigaba da kukan.. A hankali cikin sanÉ—a Ahmad ya fito yayin da ya gyara rukon bindigan sa da kyau. harbin yashiga mai da musu daga inda yake laÉ“e suka rika musanyar wuta sakanin sa da É“arayin. kara É—aya daga cikin É“arayin yayi lokacin da harbin Ahmad ya same shi, ya zube a gurin, kaimi É“arayin suka kara akan harbin da suke, cike da tafasar zuciya cikin hanzari Ahmad yafito daga in da yake laÉ“e, yana fita daga gurin kuwa wani yayi saitin sa ya sake masa harbi a gefen kirji. dafe gurin yayi cikin jin azaba da raÉ—aÉ—in shigan bulet jikin sa, cikin tsananin tafasar zuciya da kunar rai yayi gaba da gaba da su in da yakuma samin nasarar harbin mutum biyu a kafa, cike da tsananin mamaki ya tsaida harbin da yake ganin amintaccen mai gadin sa, yana nuna shi wa wasu É“arayi huÉ—u da suke tsaye da hannu,suka juyo tare da saita shi da bindiga. kafin ya dawo da ga mamaki mai haÉ—e da tunanin daya tafi, sai ji kake tau-tau saukan harbi a cikin sa har sau biyu, kara yayi tare da damke cikin sa da jini ke tsiyaya, yayi tangal-tangal kafin ya isa kasa ya harbe su gaba É—ayan su su huÉ—un nan har da mai gadi cikon na biyar, a tare suka zube kasa mutattu. yana kwance a kasa yana sakin wani irin numfashin wahala wan da yafi kama da na fitar rai... Ina zaune a kan sallaya bayan na idar da nafila kamar yadda Ahmad yace min nayi zan sami bacci, gaba É—aya ilahirin jiki na babu karfi tamkar an zare min laka. na janyo wayata lokacin karfi biyu da rabi, na danna number Ahmad tare da kara wayar a kunne na, yayi ta ringing har ya yanke bai É—aga ba, kuma mai da kiran nayi shima har na cire rai da É—aukar nasa dan nafara tunanin bacci yayi. wani irin razana da zabura nayi jin muryar sa yana faÉ—in "Kyakkyawa ta sun harbe ni sun harbe ni......! Mommyn Twins 8/19/22, 10:58 - Ummi Tandama😇: 34 Bappa yace "Allah mai girma da É—aukaka ashe dai jikata ce HAMDAH, a she dai jika ta ce nake zaune da ita cikin rashin sani, alhamdulillah masha Allah, hakika É—an adam baya fidda rai da rahamar Allah, ashe wata rana zan haÉ—u da jinina ga jiko ki na ga Æ´aÆ´a na, kuzo nan Æ´aÆ´a na Allah yayi muku albarka." ya janyo su Abbu jikin sa yana ta sanya mu su albarka, Abba ya nuna goggo Hauwa yace "Wannan ita ce kanwar mu." Bappa yace "Taho nan kema." Goggo Hauwa ta mike tana sharar kwalla taje in da yake su Abbu suka ce tabbas Inna tana faÉ—in tana da kani amma bata san in yake ba sun rabu tun suna kana na. tabbas nima Inna tasha faÉ—a min tana da É—an'uwa sai dai tun suna kana na aka raba su yanzu bata san in da yake ba.. Uncle Mahmood farin ciki ya gama lulluÉ“e shi yau shima gashi cikin ahlinsa. haka akayi ta farin ciki yayin da farin cikin ya gusar da alhinin da Na'ima ta sakawa mutane... Ahmad ya dube ni kasan cewar yanzu a kusa da shi na zauna, yace "Ina taya ki murna na karuwar ahlinki, sai naji ina ma ace nine iyayena da Æ´am'uwa na suke zagaye da ni haka." kai na rausayar ina mai jin tausayin sa, na sauke hannuna kan nashi dake saman hannun kujera nace "Allah ya haÉ—a ka da su a jannatir firdausi." murmushi yayi tare da faÉ—in amin amin.... A É“angaren Na'ima kuwa tana fita a gidan, a hargitse cikin matsanancin tashin hankali ta tsari mai napep. tayi gidan bokan ta, tana zuwa ta shaida masa abun da ke faruwa. bokan yace taje ta kawo cikiton kuÉ—in aiki yanzu ta dawo a rufawa kowa baki su mance da abunda ya faru, a kuma kashe HAMDAH. tace to ta fita abujajan ta dawo gida, domin É—aukar kuÉ—in da Raliya ta bata aro ta kaiwa boka. tana shiga gida ta dadda SALEEM a parlour da magunguna da gorar ruwa a gaban sa da alama yanzu yagama shan maganin. tana kokarin wuce sa tashiga É—aki, ya dakar da ita ta hanyar kiran sunan ta "Na'ima." ya kira sunan ta batare da ya dubi in da take ba. sai da hantar cikin ta ya kaÉ—a, jin yan da ya kira sunan nata a sama,da jin amon sautin sa da babu wasa ciki. a fusace ya mike tamkar fusataccen zaki yayi kanta, tana ganin haka ta shiga ja da baya tana kokarin gudu, da sauri ya cakfo ta tare da shako wuyan ta har saida idananun ta suka fiffito waje,yayin da numfashin ta yake kokarin barin jikin ta. wasu tagyayen maruka yashiga shinfiÉ—a mata nan da nan fuskarta ya canza kala. sai kuma ya sake ta da sauri tare da dafe kirjin sa da hannayen sa biyu, yashiga yin tari a hankali ya durkusa kasa. Na'ima ko yana sakin ta da sauri tayi baya tana maida numfashi tare da shafa wuyan ta da fuskar ta daya sauya masa kamanni... hannun sa ya É—aga yayin da taren ke ci gaba da zuwar masa ya nuna ta tare da faÉ—in "Fita tafi na daina ganin ki, ki sani har aba na haramta kaina gare ki, fita min a gida tafi na daina ganin ki, kije Allah ya haÉ—a ki da hukubar duniya dana kiyama." numfashin sa ne ya soma fizga yayin da maganar tasa tashiga harÉ—e wa. wani kururuwa Na'ima ta sake tace "SALEEM kasan abun da kake faÉ—a kuwa, kana nufin ka sake ni sakin da baza ka sake dadowa dani ba har abada, haba SALEEM kada ka min haka wlh duk abun da nayi sabo da son ka nayi, ina son ka bana kaunar wata ta raÉ“e ka sabo da son da nake maka, wayyo Allah SALEEM meyasa baka cewa HAMDAH ka haramta kanka har abada da ita ba, wayyo Allah na nashi uku dan Allah SALEEM kada ka min haka." dagudu ta juya ta shiga É—akin ta, laidar kuÉ—in da Raliya ta bata aron sa ta É—auka tana faÉ—in "Boka kai zaka iya min komai kai zaka fitar da ni cikin wannan hali, dole SALEEN ka cigaba da zama dani dole boka yasa ka ka zauna da ni." tafito da sauri, har lokacin yana durkushe dafe da kirjin sa. tayi waje da gudu, tana duba mai abun hawa, babu ko alamar su a unguwar. da kafa ta rika tafiya tana sauri kamar zata tashi sama bana ko ganin gaban ta burin ta kawai ta isa gurin boka, har ta fito babban titi zata sallaka ta koma É—ayan gefen dan ta tari abun hawa, wani mai babban mota ne ya sako kai bata ankara ba sai ji kake keeeee motar tayi ciki da ita.. salati mutane suka fara akayiyo in kan titin a can karkashin motar a ka ciro ta, gaba É—aya halittar ta ya canza sabo da sabar jin ciwo, bata ko motsi tana kwance kamar gawa. wasu suna faÉ—in ta mutu wasu suna faÉ—in bata mutu ba, aka kwashe ta aka garzaya da ita wani mafi kusa da gurin.... Da daddare duk yanda Ahmad yaso yatafi masaukin da yasa a tanar masa shi da security sa, su Abbu suka hana suka ce ya zauna a cikin dangi dan shima ya zama É—an uwa, duk da sun san gida kamar nasu kam yayi wa Ahmad Tijjani Sabil kankanta. parlour'n da su Abba suke zama su tattauna nan akayi masa masauki, kasan cewar akwai bedroom's ciki har guda uku, shi É—aya Bappa É—aya Uncle Mahmood É—aya. sashin Inna na gidan kuma akayi wa security masauki ciki, inda mu mata kuma muke cikin sauran sashin wato sashin Ummi da Mamie, dan su Aunty Rafee'at ma anan gidan yau sukace zasu kwana.... Washegari duk a sashin Mamie muka hallara kamar jiya, anan mukayi breakfast, ana zaune ana ta hira, Bappa yace a kira masa Ya SALEEM kowa na nan shine kaÉ—ai ba ya nan, ya kama ta yazo ya gan sa dan ganin da yayi masa jiya ko a hanya ya gansa yanzu bazai gane sa ba. Ya Masa'ud ne ya kira sa a waya ya É“ata lokaci mai tsawo kafin yazo. yashigo sanye da kananun kaya a jikin sa Black jeans da yellow t-shirt. kallo É—aya nayi masa na É—auke kai, ya É—an rame ya kara haske gashin kan nan nasa nanan yalan-yalan baki sutuf sai sheki yake, sai dai ya É—an hargitse da alama bai sami damar tace shi ba ya fito. fuskar nan tasa a É—aure tamau yanayin nan nasa da yanayin suffarsa yana nan yana biye da shi. Bappa yace "Zo zauna nan kusa da ni SALEEM kaga yan da Allah yake ikon sa ko ashe ku jinina ne." Ya Masa'ud ya washe baki yace "Ya SALEEM ashe shine kanin Inna da take faÉ—an nan, jiya kawai sai gashi da É—ayan wancan hoton Inna." ya nuna hoton ta dake like a jikin garun parlour'n yana mai cigaba da washe baki cike da farin ciki. shiko Ya SALEEM bai yi magana ba sai zama da yake a kuje rar gefen Bappa, duk maganar da ake baya jin su gaba É—aya hankalin sa na kan su Naseem da suke jikin Ahmad. waya ta na É—aga nashiga daddan na ta, ina jiyo gaisuwar da yake yiwa su Bappan kamar mai ciwon baki. su Aunty Rafee'at suka gaishe sa, ya amsa kamar wanda aka sashi dole. baki na taÉ“e a kasan raina nace ashe dai hali na nan. Ahmad ya mika masa hannu da murmushi kan fuskarsa yana faÉ—in "Barka da safiya." "Barka." kawai yace a dakile batare da ya dube sa ba bare ya sa ran zai karÉ“i hannun nasa suyi musabaha. Naseem da ya kafe Ahmad da ido yana kallon yan da ya mika wa Ya SALEEM hannu, sai ya washe baki shima ya miko masa hannu tare da faÉ—in "Baika ka da wai haka." dariya duk aka saka ganin yan da yayi kamar wani babba, shima dariyar yayi yace "Daddy haka ake yi." kai Ahmad ya gyaÉ—a masa yana dariya. Ya SALEEM kuwa tun da Naseem ya miko masa hannu yakafe tafin hannun nasa da ido, har ya janye hannun yana binsa da kallo yayin da jikin sa da zuciyar sa suke wani irin fizga da jin yaran a cikin jikinsa. Ya masa'ud ne ya miko masa hannu yace "Zo mu gaisa my boy." ai ko da gudu suka dawo jikin Ya Masa'ud Nasmah tana faÉ—in "Hai dani Uncle." hannayen su duka ya rike yana yi musu dariya yace "To munyi gaisuwar." jiki na suka dawo Naseem yace min "Mommy ya sunan shi?." ya nuna Ya SALEEM. yi nayi kamar banji sa ba, ina cigaba da danna waya ta. ganin ban kula shi sai ya shiga bubbuga kafa kasa yana faÉ—in "Mommy ya sunan shi ni ban sani ba." batare da na É—ago daga kallon wayar da nake ba nace "Uncle." Nasmah tace "La shima Uncle ne." sai suka juya suka ci gaba da tsalle-tsallen su a sakiyar parlour'n. Ahmad ya mike tsaye sakama kon shi gowar kira wayar sa, ya É—aga kiran yayi waje. Nasmay ce ta bi bayan sa tana faÉ—in "Daddy nima dan bika." yace "Waya zanyi Nasmah ina zuwa." tace to sai ta dawo. goggo Hauwa ta dube su cike da sha'awar yaran ta dube ni tace "Allah sarki HAMDAH wai nikam ina cikin da kika tafi dashi ne kam, ko wuya ya sashi zuba ne, tun jiya nake ta son na tambaya." Aunty Rafee'at tayi murmushi tare da kallon yaran tace "Gasu nan Naseem da Nasmah takwaran Inna da Abbu." wani irin É—ago wa Ya SALEEM yayi yana mai ware idanunsa a kan yaran yana binsu da wani irin kallo. goggo Hauwa ta janyo yaran tana faÉ—in "Ikon Allah ikon gaske Allah mai girma ashe dai kune Æ´aÆ´an SALEEM." da sauri na É—ago tare da faÉ—in "Su ba Æ´aÆ´an sa bane Æ´aÆ´a na ne!." Ummi tace "Ke HAMDAH baki da hankali ne." da sauri Mamie ta tari numfashin ta tace "Da hankalin ta karya ta faÉ—a ne?." mike wa nayi na dubi su Nasmah nace "Ku wuce muje nayi muku wanka." ai ko da gudu suka riga ni fita na bi bayan su muka nufi sashin Ummi. A parlour'n kuwa murmushi Abbu yayi kana yace "Yarin ya ta faÉ—i gaskiya Æ´aÆ´an ta ne tafi kowa iko da su ita tasan wuyan su, sannan kuma ai da bakin sa yace ba cikin sane, ta ya za'ayi su zamo nashi." wani irin mike wa Ya SALEEM yayi yanufi kofa yayi waje. Abbu ya bi bayan sa da kallo yana jinjina kai.. Muna shiga side Ummi kuwa bedroom na shige da su muka haye gadon Ummi, nace "Ku zauna a nan kuyi wasan ku." nima nayi kwanciya ta. kwanciya ta bada jimawa ba kiran Ahmad yashigo waya ta ina É—agawa yace "Kyakkyawa ta kina ina nashigo ban ganki ba?." "Ina side É—in Ummi." yace "Shine kika bar Ahmad yana kuka zo ki karÉ“e sa." nace to. kana na mike na fito. ina fita na hango sa shima yana fito wa daga sashin Mamie rike da Ahmad karami a hannunsa sai dariyar sa yake, tsayu nayi dai-dai kofar Ya Masa'ud ya karaso tare da miko min shi yace "KarÉ“e shi ki bashi nono." baki na turo nashiga yarfe hannu ina É—an bubbuga kafafu na a kasa cikin muryar shagwaÉ“a nace "Dama ba kuka yake ba kace wai yana kuka yaro yana wasan sa, baya jin yunwa." yace "A'a kyakkyawa ta bashi nono yasha tun É—azu da yasha ina lura baki kuma kara masa ba, yana da hakuri ne kawai shi yasa baiyi kuka ba." "Allah ni nagaji da shan nonon nan har zafi yake min fa." yace "Yi hakuri muje na hura miki shi zai daina zafin, muje na gani, idan ya daina sai ki bashi ya sha." yayi hanyar side É—in Ummi, na É—aga kafa zanbi bayan sa, sai naji tari cikin É—akin Ya Masa'ud kofar É—akin na tura ina faÉ—in "Ya Masa'ud wannan irin shakewa haka kasha ruwa mana ko..." nayi maganar ina leka cikin É—akin, cak na haÉ—e ye ragowar maganar tawa ganin ba Ya Masa'ud É—in bane Ya SALEEM ne yana dafe da kirjin sa, ina sako kaina idanunmu ya sarkafu da juna, da sauri na janye nawa baya nayi da sauri nabi bayan Ahmad... muna shiga ya zauna kan kujera na zauna gefen sa, yaja riga ta sama ya ciro nonon cikin bra ya É—aura shi kan kafa ta, yasaka masa cikin baki yaleko fuskarsa yace "Sha a hankali bada zafi ba." hannun na ya ruko ya haÉ—e cikin nasa, ya dube ni tare da faÉ—in "Kyakkyawa ta gobe zamu koma ko." ido na waro nace "Gobe kuma." kai ya gyaÉ—a yana murmushi baki na turo nace "Ni da zan yi wata uku." yace "Wata uku? ina ban isa ba, in kin daÉ—e kiyi sati É—aya, gobe ni zan koma akwai abin da zanyi sati É—aya zakiyi kuma kinci kwana biyu a ciki." "Haba My sati É—aya yaushe naje na yi ziyara har Dass fa zani, ni da nake so ma na wuce har Maiduguri garin su Ummi, sati 1 ai ba zai min ba." "Kidai je Dass amma banda Maiduguri kibari zamu je musu na musamman,sati É—aya babu kari, bari naje naga gari." yayi maganar yana mike wa. nace "Nidai sati 1 ya min kaÉ—an,wata É—aya zanyi." yace "Ni dai natafi ganin gari." "Idan ka É“ata babu ruwa na." waje yayi yana dariya da faÉ—in "Idan har na É“atan ke zaki fara nima na." bayan sa nabi lokacin har yayi waje da sauri haÉ—e da sassarfa na iso in da yake naruko hannunsa ina dariya nace "Ko neman ka bazan yi ba idan ka É“ata." shima dariyar yayi tare da jan kumatu na yace "To sake ni naje na É“atan." kafaÉ—a na make ina kwantar da kaina a kafaÉ—ar sa nace "A'a to ai ina son ka idan da bana son ka ne sai na barka ka tafi kaje ka É“atan." kiss ya manna min a gefen fuska a hankali yace "Ko zamu tafi tare ne Allah nayi missing É—in ki." dasau ri na É—ago kai na ina kokarin barin gurin da sauri ya ruko hannun ya janyo ni yace "Muje ni?." kai na girgiza ina dariya nace "Jeka kawai." "Zo kiji wani magana." yafaÉ—a yana kokarin haÉ—e jikin sa da nawa, yayin da hannunsa ke sarkafe cikin nawa dukkan mu dariya muke ina É—ago wa muka haÉ—a ido da Ya SALEEM,dake tsaye jikin motar sa da waya kare a kunnen sa da alama waya yake. kai na nakawar tare da mai da dubana kan Ahmad nace "My ina fashin salla fa." "Zo muje na gani da ido na." da sauri na fizge hannuna na juya ina yi masa dariya na koma ciki.. a É“angaren Ya SALEEM kuwa da sauri ya shige motar sa ya bargidan da mugun gudu kamar zai tashi sama.... Washegari da safe Ahmad da Uncle Mahmood da iyalen sa suka juya, sabo da ai kin sa. washegari nima na tafi Dass ni da in da Ya Masa'ud da Fauzan da Nusaiba suka yi min rakiya. ranar da muka isa Dass nasha kuka gani na É—akin Inna ta bata nan ciki. na zaga gida jen Æ´an uwa da abokan arziki tun da nazo muna yare da kawata Rabi da yanzu Æ´aÆ´an ta biyar, ranar da zamu dawo Bauchi ta raka ni lambun Baba na lambu, muka same sa yana ta ai kin ban ruwa wa kayan lambun sa, ko da ya ganni bai gane ni ba sai da Rabi ta tuna masa ni. yace "Allah sarki HAMDAH kece kika zamo haka sam ban gane kiba." nayi murmushi bamu bar gurin ba sai da muka tuno da da na cire mayafi na nasha É—ammara na karÉ“i tiyo nayi ta bin layi layi ina zubawa shukan ruwa, cike da nishaÉ—in tuno da baya. kuÉ—i na bashi masu yawa nace ya kara jari da su. yayi ta min godiya yacire min kayan miya yacika min babban laida da su yace naje na sha miya.. Rabi da Mamar ta duk sai da nayi musu alkawarin, musamman Rabi da naga kalar yaruwar da take kuÉ—i masu yawa na bata nace taja jari da su tasami abin dogaro da kai ita da Æ´aÆ´an ta, nakuma bada kuÉ—i domin a sasu a makaranta dan duk basu makaranta kuma sun fi su Naseem girma, muka juyo Bauchi.. ranar da na cika sati Ahmad yakira ni wai sai dai na taso yau nace dan Allah ya barni na kara wani satin. da kyar ya amince nayi kwana goma, shima É—in sai da ya haÉ—a da Ummi da kanta ta shirya mana kayan mu, ta sa aka kai mana cikin mota. Ya Masa'ud ne ya shigo ina gyara mayafi na Ummi tana ta cewa nayi na fita kada muyi tafiyar dare, kada na bi na su Aunty Rafee'at mu É“ata lokaci. hannun su Naseem ya kamo yace "Wai ku zo." ya janyo hannunsu har sun kai bakin kofa nace "Ya Masa'ud wake kiran su?." "Ya SALEEM ne." yayi maganar suna fita daga parlour'n. da sauri na bi bayan su Ya SALEEM É—in yana tsaye jikin motar sa su kuma suna daf da isa in da yake. sauri na kara na iso su narike hannayen su tare da janye su nace "Ya Masa'ud kar ka kaisu sauri muke." sai na juya gurin mota na buÉ—e na saka su ciki nima na shiga na mai da murfin motar na rufe. yabi motar da ido. su Bappa suka fito da duk mutanen gidan in da su Bappa suka shige motar da suka zo ciki. Ummi tazo gefen da nake ta buÉ—e ta mika min Ahmad tana yi mana fatan isa gida lafiya, muka yi bankwana da Æ´an uwa har muka fita yana nan tsaye a gurin..........! 8/19/22, 10:58 - Ummi Tandama😇: 36 A kiÉ—ime na mike tsaye ina faÉ—in "My me ya same ka suwaye suka harbe ka My me ya same ka My kayi magana dan Allah!!!." numfashi yaja da kyar cikin sarkewar murya yace "Nasan bazan rayu ba sun illatani da yawa, kiyi hakuri kyakkyawa amma ki sani da son ki zan mutu ina son ki ina son ki." ya karasa maganar da jan wani irin. numfashi hade da yin salati. kuka sosai na fashe da shi ina faÉ—in "My kar kayi min haka dan Allah kada ka tafi ka barni dan Allah, ka jira ni zan zo yanzu babu abun da zai same ka zan zo yanzu gani zuwa My kana jina ka jira ni kaji, babu abun da zai same ka." cikin yanayin jin azaba da fitar numfashi yace "HAMDAH kada ki zo kinji kyakkyawa ta akwai wan da basu mutu ba a cikin su bazan juri ganin sun nimi illatar da ke ba, na rokeki kibarni natafi cikin salama bada kunar ran abun da zasu yi miki ba, kada ki bari Ahmad yayi kukan maraici." maganar tasa ce ta sarke yayin da yaja wani irin numfashi mai haÉ—e da ajiyar zuciya kana salati yabiyo baya. "Myyyyyy!!!." na kira shi da karfi jin alamar faÉ—uwar wayan kasa, nakuma sakin wani irin kuka mai tsuma rai. da gudu nayi waje a kiÉ—ime ina kuka da kiran sunan sa ina faÉ—in kada ka tafi ka barni. a haka nafito sakar gida yanayin dare shiru babu motsin kowa, sai hasken daya haske ko ina na gidan. masu gadi suna can bakin get, kuka mai karfi na sake san da na kuma kiran wayan sa a karo na uku ba'a É—agawa, direba nashiga kwallawa kira cikin muryar kuka mai haÉ—e da tsantsar tashin hankali, da iya karfi na nake kiran direba. da gudu su security da direba suka iso in da nake a tare suna tambayar ko lafiya akwai wata matsala ce. ban iya basu amsa ba sai cewa direba nayi "Bani makullin mota." direba yace "Ina kuma zuwa hajiya da daddaren nan yanzu fa karfe uku saura shin lafiya?." cikin muryar kuka da karfi nace "Ka bani makullin mota nace." jin hayaniya yasa su Bappa fitowa daga sashin su Mama mai awara ma haka ta fito daga É—ayan side É—in dasu Talatu, da sauri suka karaso in da muke hankali tashe Bappa da Inna Wuro da Mama suka haÉ—e baki wajen cewa "Lafiya me ke faruwa?." ganin yan da na birkice gaba É—aya Bappa ya ruko hannuna yana faÉ—in "HAMDAH ki nutsu mene ne a cikin sashin naki ina yaran suke?." cikin jan shassheka nace "Bappa Ahmad Ahmad zasu kashe shi." cikin matukar shiga firgici Bappa yace "Su waye zasu kashe shi ina Ahmad É—in yake kin baro shi a É—aki ne?." a zaton sa Ahmad karami ne. nace "Yana gidan sa Bappa sun harbe shi." kuka ne yaci karfi na nashi kokarin kwace hannuna Bappa yarike ni gamgam yana faÉ—in "Innalillahi wa'inna'ilaihirraji'un ki nutsu HAMDAH ki tsaya tukun ba zai yiwu kifita a daren nan ba, ki bari hukuma suje dan zuwan naki akwai hatsari." Bappa ya dubi security yana faÉ—in "Kuje gidan ku kai masa É—auki." da sauri suka juya cikin zafin nama cikin hanzari suka shige motocin su suka nufi gidan Ahmad. Bappa ya dube ni ganin yan da nake rusar kuka yace "Jami'an sa ne dama shi ya ajesu a gidan nan batare da saninki ba zasu je su kula dashi, babu komai in sha Allah babu abun da zai faru, ki kwantar da hankalin ki yanzu zasu je suzo miki da shi." da kyar suka lallaÉ“a ni na yarda muka koma ciki... Acan cikin gidan Ahmad tuni wani makocin sa yayi waya wa jami'an tsaro dan gaba É—aya unguwar ta É—auka, sai dai babu wan da yayi yunkurin fita dan jin yan da karan bindiga ke tashi, sai dai kowa yana tsaye a kan kafafun sa a cikin gidan sa. kan kace me sojoji sun iso unguwar suka zagaye gidan, koda security suka iso sun tadda sojoji a gurin, nan suka haÉ—e da sojojin. wasu daga cikin jami'an tsaron suka shiga cikin gidan. Rasheedat na É—aki tana ta rusar kuka, jin harbin bindigan ya tsaya ba'a kuma yi ba daga bisa ni tajiyo jiniyar sosoji, sai ta buÉ—e kanta tafito hankali. wani irin kaÉ—uwa tayi ganin Ahmad kwance cikin jini, tayi kansa tana ihu da kiran sunan sa, tana faÉ—in "Aboki sai da nace maka kar ka fito ka fita ta kofar baya wayyo Allah na karkayi min haka Aboki." polisawan da suka iso yanzu suma motar su guda su suka dakar da ita batare da sun barta ta taÉ“a shi ba, sabo da yanayin ai kin su da kuma gudanar da aikin su da suke a lokacin. ta zube a gurin tana rusar kuka mai ban tausayi. abun mamaki duk hayaniyar da ake É—inan security suna ta sharar bacci karnukan gadi kuma suna zaune in da suke tun É—azu basu ko mosa ba bare suyi haushi. motar ambulance da ta iso yanzu cikin hanzari polisawa suka É—auki Ahmad suka saka shi cikin motar, in da wasu daga cikin police É—in duka shige cikin motar da mugun gudu motar ta fice a gidan. sauran gawawwakin É“arayin dake kwance har da mai gadi suma a ka zuba su cikin wata mota aka tafi da su, É“arayi biyu kuma da suke da rai wan da Ahmad ya harbe su a kafafun su a ka zubasu cikin wata mota suma a ka tafi da su... kan kace me a cikin daren unguwar gaba É—aya ta gama hargitsewa hankalin kowa ya tashi da jin abun da yafaru, matasa suka fito kowa da makamai nan karamar zanga-zanga ya kaure, sai da hukuma sukayi da gaske. a take a lokacin labari ya iske mahaifan Rasheedat hankali tashe suka iso gidan a cikin daren, Alhaji Bashir mahaifi ga Rasheedat kani kuma wa Alhaji Tijjani Sabil,Bappan Ahmad kenan, hankalin sa yayi mummunar tashi a take yabi bayan motar da aka tafi da Ahmad, in da mahaifiyar Rasheedat kuma ke tare da ita agidan.... sai da aka kira sallar asuba kafin security suka farka duk tulin bubbuga su da sojojin da suka zo sukayi domin su farka baisa sun farka ba sai a lokacin, karnuka ma suka kama haushi da tsalle kamar zasuci babu. hankalin security'n yayi masifar tashi da jin abun da ya faru wan da suna cikin gidan basu kuma san da faruwar hakan ba. koda Æ´an jaridu suka nimi jin ta bakin su sun shaida musu cewa su sam basusan da faruwan komai ba sun dai sinci kansu cikin yin bacci mai nauyi, bayan da mai gadin gidan ya rabamusu lemun gora a daren ranar yakuma shaidar musu da cewa ogan su ne ya bashi ya basu wato Ahmad É—in kenan, shan su kuma bada jimawa ba bacci mai nauyi ya É—auke su, wan da basu farka ba kuma sai yanzu. É—aya daga cikin security ya bada tabbacin cewa shi bai sha lemun da wuri ba ya aje nashi sai daga baya yasha, lokacin da bacci ya fara fizgarsa bai kai ga É—aukar sa ba yaga mai gadin yaje in da karnuka suke yana fesa musu wani abu, sai dai baccin da ya zo mishi babu zato ya hanashi tashi ya bincike mai gadin kan abun da yake yiwa karnukan... har gari yayi haske sosai sojoji na zagaye da gidan, tuni gidajen TV dana rediyo suka fara sakin labarai kan rahoton da suka samu..... A parlour mukayi salla dukan mu har da su Bappa, dan Bappa yaki matsawa ko nan da can daga in da nake. ganin gari yayi haske kuma har zuwa lokacin security basu zo da Ahmad kamar yadda Bappa ya faÉ—a ba. gashi duk kiran wayar sa da nake baya É—agawa, na saka musu kuka nace ni sam zan tafi zanje da kaina gidan. wayar Bappa ce tayi kara, ya É—aga tare da yin sallama. "Innalillahi wa'inna'ilaihirraji'un." abun da Bappa ya furta kenan, zumbur na mike tsaye ina kallon Bappa, Bappa ya kawar da kansa tare da sauke wayar a kunnen sa, yayin da laɓɓan sa ke motsawa alamun salati yake. É“ari jikina ya soma murya na rawa nace "Bappa mene ne wa yayi maka waya?." kai ya girgiza yayin da idanunsa suka kawo kwalla, sai ya kawar da kansa daga kallo na yace "Babu komai je ji sa babban mayafi ki zo sai muje gidan Ahmad É—in kawai tun da har yanzu basu zo ba." ya dubi Inna Wuro yace "Je ki rakata tasa mayafin." sai ya sauya harshen sa izuwa fulatanci yayi mata magana cukin harshen fulatanci, Inna Wuro ta saki salati tana dafe kirji, sai kuma tayi saurin sauke hannunta a kirjin sabo da maganar da Bappa ya kuma mata da fulatan ci, ta ruko hannuna yayin da hannunta ke É“ari ta janyo ni muka haura sama. muna shiga muka tadda su Naseem duk sun farka, tace na cire hijabi da kayan baccin da ke jiki na na sa wani kayan. jiki a sanyaye yayin da hawaye ke bin fuskata nayi kamar yanda tace, nasaka babban hijabi, kana ta ruko hannun su Nasmah ni kuma na É—au Ahmad karami muka sauko kasa. tun kan mu karaso parlour'n kasa su Mama suna ganin mu kowa ya shiga sun kuyar da kai suna share hawayen su cikin dabara sai kowa ya mike da sauri akayi waje gaba É—aya. da sauri na É—aga murya nace "Kukan me kuke yi?." da sauri Bappa yace "Kuka kuma sam ba wan da yayi kuka a cikin mu." cikin rawar murya da kuka ke son kwace min nace "Na ganku da idona na, ganku kuna kuka ku faÉ—a min kukan me kuke yi?." Mama tayi murmushi wan da yafi kuka ciwo tace "A ina kuma HAMDAH mu sam bamuyi kuka ba muje direba yana jiran mu." ta ruko hannuna muka karasa fita waje... koda muka iso parking lot Bappa yace su Zulai su zauna da su Naseem a gida. a tsakiya suka sani Mama da Inna Wuro, Ahmad karami na rike a hannu na, Bappa kuma ya zauna a gefen mai zaman banza, direba yaja muka fita. ina zaune shiru hawaye na zuba a idona na, ido na kurawa titi ganin mun É—au wata hanyar daban ba hanyar gidan Ahmad ba. a bakin wani katon asibiti direba yayi hon, aka buÉ—e masa ya sakai ciki ya faka motar muka fito, asibitin zagaye yake da sojoji da Æ´an sanda, can na hango Abba Bashir yana sunkuye da alamar kuka yake, wasu mutane na tsaye a kansa. Inna Wuro ta karÉ“i Ahmad karami dake hannuna, Mama kuma ta ruko hannuna gam ta janyo ni muka nufi cikin asibitin. da kyar nake iya É—aga kafafu na da sukayi min mugun nauyi, maganar Mama na jiyo tana faÉ—in "Ba a ja da ikon Allah duk abun da kaga ya sami bawa da sanin ubangiji, Allah kuma baya barin wani dan wani yakan kuma jarabci mutum ta ko wace hanya domin ya gwada imanin sa, yana da kyau mu kasan ce masu karÉ“ar kaddara mai kyau ko mara kyau aduk san da tazo mana, Allah yafi mu son bayin sa duk son da muke musu, hakuri kuma shine magani nasan ki da hakuri da iya karÉ“ar kaddara ina fata yau ma ki kasan ce a haka, kice Innalillahi wa'inna'ilaihirraji'un kici gaba da nanata shi cikin ranki." "Innalillahi wa'inna'ilaihirraji'un³." nafaÉ—a da karfi har sau uku dai-dai lokacin da muke sakai cikin parlour'n asibitin, Mama ta daÉ—a rike hannuna gam jin yan da ilahirin jikina yaÉ—au ki É“ari tace "A hankali zaki faÉ—a ko a cikin ranki ki nusu HAMDAH." muna shiga jami'an tsaro suka dakatar da mu suka ce mu tsaya anan, wani soja ne ya fito daga cikin wani room yakaraso in da muke yace "Zata iya shiga yanzu." Bappa ya dube ni cikin rauni yace "Kullu nafsin za'ikatulmaut duk mai rai mamuci ni, muma bamu da tabbacin zamu iya kaiwa nan da dakika É—aya, Allah yayi wa Ahmad rasuwa ki daure kiyi masa addu'a." wani irin dimm haka naji kunnuwa na sunyi min mugun nauyi jiri haÉ—e da bakin duhuwa ya gilma min, kallon bakin Bappa nake domin tabbatar da abun da yake faÉ—a dan ni dai a yanayin da nake jin kaina ciki da yan da maganar tazo min a sama sai ji da gani nake kamar ba gaskiya bane, bakina kuma yayi min mugun nauyi na kasa iya furta komai. sojan yace "Madam bismilla sai hakuri fa." yayi maganar yana nuna min hanya Inna Wuro ta mika min Ahmad karami, kana sojan yayi gaba na bisa a baya ina jan kafata da kyar. muna isa jikin kofar room É—in ya murÉ—a handle É—in ya shiga, kana yaÉ—an ja gefe ya bani hanya na sako kai na ciki. kana ya mai da kofar ya rufe, sojoji ne tsaitsaye cikin room É—in haÉ—e da likitoci, ido na kurawa kan gadon da nake hango mutum kwance an lulluÉ“e shi daga sama har kasa, jikin a bun da aka lulluÉ“e sa da shi da É—igo É—igon jini tagurin kirjin sa da gefe da gefen cikin sa. wani dake tsaye ta gurin kansa ga dukkan alama babbane dan da zaran yayi magana sai sauran jami'an tsaron su sara masa. ya É—aga hannu tare da yi min alama dana karaso, a hankali naja kafafu na zuwa bakin gadon, ya dube ni tare da faÉ—in "Allah ya baki hakuri mun kira ki ne abisa cika masa burin sa na karshe, kiyi hakuri bamusan rai zaiyi halinsa ba tun a daren jiya yanemi da a kira ki sai dai ganin halin da yake ciki yasa muka kasa iya ai watar da hakan burin mu kawai likitoci su samu nasarar kuÉ“utar da shi daga halin da yake,ga wannan a hannunsa muka samu bayan cikawar sa, ko da muka duba sai muka ga a kanki yake maganar shine muka neme ki kafin mu É—aga shi a nan mu damka miki sakon sa a hannun ki." ya mika min takarda wan da gefe da gefen takar dan duk da É—igon jini, hannu na na É“ari na karÉ“i takardan na dunkule shi cikin hannuna. mutumin ya dubi nakusa da shi yace "Ku buÉ—e mata shi ta gansa." ya yaye abun da aka rufe shi da shi daga kansa zuwa wuyan sa. da gaske Ahmad ne a kwance wan da tun É—azu ban gaskata abun da suke faÉ—a min ba sai gani nake kamar ba gaskiya bane. wani irin tsalle zuciya ta yayi tamkar zai faso kirji na yafito,yayin da ilahirin jiki na ya É—auki É“ari. a hankali nashiga jan kafata ina daÉ—a matsowa bakin gadon yayin da idanuna ke kan fuskarsa, yana kwance idanunsa a rufe yayin da fuskarsa ke bayyane da kayataccen murmushin sa, tam kar akirasa ya amsa. kai na shiga girgizawa nashiga kokarin motsa laɓɓa na, na mika hannu izuwa jikin sa, nashiga girgiza shi tare da sakin kuka mai taÉ“a zuciya cikin muryar kuka sosai tamkar numfashi na zai fita nashiga faÉ—in "My bana son irin wannan wasan!, My kafarka dan Allah kadai da min irin wannan wasan,ka tashi mana nice fa gimbiyar ka kyakkyawar ka, ka tashi ka gani gani ga Ahmad É—an ka É—an da ka fara samu a duniya, shin ka mance alkawarin da ka min da bakin ka kace min bazaka taÉ“a bari nakara yin kuka ba, kar kayi min haka kar ka tafi ka barmu dan Allah My dan Allah ka tashi so kake Ahmad ya zamo maraya, ka buÉ—e idanun ka ka faÉ—a min kalmar da kake faÉ—a min kullum kana sona nima ina son ka My ina sonka ina sonka My, My ka tashiiiiiiiii kar ka mutu dan Allahhhhhhhhh!!!." kuka yaci karfi na sai kawai na kife kansa tare da É—aura Ahmad karami a kansa na saka fuskata kan nashi nashiga goga fuskata cikin nashi ina wani irin kukan danake jin ina ma ace yanzu nima na mutu na bishi, Ahmad karami ya saki kuka yana cakumar sa... mutumin da ya sa aka buÉ—e min shi ya girgiza kai tare da share kwalla, kana yace "I'm so sorry Madam hakika muma munji É—acin rasa gwarzon jami'in sirri kamar Ahmad, sai dai abun farin ciki duk da bulet har uku da suka same sa a gurare daban-daban wan da ko da ace harbi É—aya ne bazai iya taÉ“uka komai ba, amma da bulet É—in a jikin sa ya kashe mutane biyar yayi wa biyu mummunar raunin da bazasu iya morar raruwar su ba, hakika wannan abun alfahari ne, Allah ya baki hakuri." sukace na tashi a É—aga shi fir naki sai ma daÉ—a kankame shi da nayi. da kyar babban sun ya iya janye ni a jikin sa,ina mike wa a jikin sa sai ji nayi tamkar an fisgo ni sai kawai na yanki jiki na zube a gurin nan take hankali na yabar jiki na ban kuma sanin abun da ake ciki ba.... After 5 hr. Sai a lokacin na farka daga doguwar sumar dana tafi, a hankali nashiga buÉ—e idananuna dasuka yi min mugun nauyi, maganar Ummi na najiyo a kusa da ni, da sauri na yunkura zan mike, Ummi tayi saurin rike ni tana faÉ—in "Yi a hankali HAMDAH." nace "Ummi ni tashi zanyi." Mamie dake zaune a gefe da waya a kunnen ta tana faÉ—in "Mun iso sai dai har yanzu bata farfaÉ—o ba." sai kuma tayi saurin kashe wayar ta mike tazo ta rike ni tana faÉ—in "Zaki iya tashi?." kai na gyaÉ—a, tace "To tashi." suka taimaka min na mike zaune, kokarin durowa a gadon nake Ummi tace "Da kata HAMDAH ina zaki ko fisari kike ji?." kuka na fashe da shi nace "Ni gun Ahmad zan je." hawaye Ummi ta share Mamie tace "Kiyi hakuri HAMDAH, ki tsaya ki daÉ—a samin sauki tukun." kai na shiga girgiza wa ina faÉ—in "A'a ni gurin sa zanje ni dai zanje." duk yan da suka kai da lallaÉ“i na fir naji nace nidai gurin sa zani, haka suka hakura suka kyale ni. na sauko a gadon da gudu nafita a room É—in, nashiga waige-waige room É—in da aka kwantar da Ahmad na nufa a guje na tura kofar na shiga, turus nayi cikin É—akin ganin babu kowa ciki. sai kuma na juya a guje tare da kuka sakin kuka nayi, su Ummi da suka biyo baya na suka ruko ni. Mamie ta rike ni gam tana faÉ—in "Ki nutsu HAMDAH." nace "Ni gida zan tafi an mai da Ahmad gida nidai gida zanje." Su Mama Inna Wuro Ummi Mamie duk kanin su hawaye suke cike da matukar tausaya min, Ahmad karami na goye a bayan Mama yana bacci sai sauke ajiyar zuciya yake. Mamie tace "To muje gidan... ko da muka iso gida direba na dai-dai ta parking na fito da gudu nayo cikin side É—i na,tun daga parlour'n kasa nake faÉ—in "My kana ina My kadawo gida ko." har na haura sama ban fasa kiran sa ba, na shige bedroom ina ta waige-waige. Ummi data biyo baya na da sauri ta ruko ni tana faÉ—in "HAMDAH kidawo cikin hayyacin ki, ki nutsu kiji ni, Ahmad ya rasu mutuwa kuma ba karya bace, yanzu addu'a kaÉ—ai yake bukata shi da ma yayi kyakkyawar tafiya ki nutsu ki sawa zuciyar ki salama ki fauwalawa Allah komai, hakika akwai ciwo amma ki daure, ki daure jin Æ´ata Æ´ar albarka Allah ya baki ikon cin jarabawar ki." "Ummi yanzu shima ya tafi kenan bazan sake ganin sa ba kenan Kamar Inna." kwai Ummi ta shiga girgiza wa tana kwalla. rungume Ummi nayi tare da sakin wani irin kuka, bata hanani yin kukan ba sai bubbuga bayana da take itama tana kwalla. su Mama suka janye ni a jikin ta suka zaunar dani bakin gado na zube a gadon ina mai ci gaba da rusar kukan.. Basu hanani kukan ba sai da nayi sosai kafin suka fara rarrashi na, da ban baki har nayi shiru,sukayi ta bani baki haÉ—e da nasihohi nidai ina nan zaune amma hankali na baya gurin, nan Ummi suke shaida min tare suka zo da su Abbu suna gidan Ahmad can in da ake zaman makoki... Bayan kwana uku..........! Mommyn Twin ce 8/19/22, 11:01 - Ummi Tandama😇: 37 Haka zan rungume Ahmad karami nata kuka cike da tausayin sa da kuma tausayin kaina,sai Mamie ko Ummi sun karÉ“e sa, tun ranar da Ahmad ya rasu Ahmad karami yaki shan nono, Ummi tace a É—aga shi kawai a nonon tun da ya makai na yaye... A ko da yaushe su Ummi suna tare da ni basa taÉ“a barina na zauna ni kaÉ—ai,yau su Aunty Rafee'ta suka zo ita da Aunty Jaleela da Ya Masa'ud da Goggo Hauwa, da yamma suka É—unguma suka je gidan Ahmad domin yi wa Æ´an uwan sa da Aunty Rasheedat ta'aziyya har da su Mamie. kamar yadda suma Æ´an uwan nasa suke zuwa har dama Æ´an uwan Aunty Rasheedat domin yimin ta'aziyya. Abba Bashir da mahaifiyar Aunty Rasheedat su tun ranar rasuwar ma suka zo nan.. tare da su Abbu su Ummi suka dawo dan yau an gama zaman makoki... ranar bakwai da safe Alhaji Bashir da mahaifiyar Aunty Rasheedat da ita Aunty Rasheedat É—in da wasu daga cijin dangin su, da shaidu da kuma laiyoyi, da manyan malamai suka zo. duk kanin mu muka hallara a parlour'n kasa. Aunty Rasheedat na rungume da Ahmad karami a jikin ta, ta kura masa ido sai kawai ta fashe da kuka, ni ma kukan na fashe da shi dan nasan abun da nake ji a raina itama shi take ji. rarrashin mu akatayi tare da yi mana nasiha har sai da zuciyoyin mu suka sami salama, kana a ka soma gudanar da abin da ya taramu wato rabon gado. duk kanin dukiyar Ahmad da kaddarorin sa na nan gida Nigeria da kuma na kasashen waje da wan da aka kashe shi domin sa wan da ya damkawa manajan banki, duk aka haÉ—o kansu. batare da É“ata lokaci ba malamai suka fara gudanar da rabon gado kamar yadda shariya ya shar'anta, duk kannnin mu uku a ka dan kawa kowa abin da ya gada ni Aunty Rasheedat da kuma Ahmad karami, nayi mamakin tulin dukiya da kandarorin da Ahmad karami ya gada, daga mahaifinsa nakuma yi mamakin tulin taren dukiya irin na Ahmad. Washegari su Abba Abbu Mamie Aunty Rafee'at Aunty Jaleela Ya Masa'ud suka koma Bauchi, yarage saura Ummi na, Ummi tana iya bakin kokarin ta wajen ganin ta gusar min da damuwa ta dan ko nan da can bata matsawa koda yaushe tana tare da ni. yanzu Mama ma ta dawo side É—ina ita ma muna tare.. lokacin da mukayi arba'in Ummi tace zata koma gida, washegari bayan ta gama shiri ta je sashin su Bappa bayan sun gaisa take sanar masa yau insha Allah zata koma sannan ta É—aura da faÉ—in "Bappa ina so na tafi da HAMDAH tadanje tayi kwana biyu." Bappa yace "Kwarai kuwa kinyi tunani me kyau tafiya da ita É—in shiyafi saboda acan zata zauna cikin yan'uwanta da iyayenta tunaninta zai ragu akan zamanta anan É—in, Allah yatsare yakiyaye hanya." Ummi ta amsa da Amin... ina zaune dasu Naseem da Nasmah suna gefena sai rikici suke min kaman kullum Naseem daya ware baki zaiyi kuka yace " Mommy ina Daddy kince zai dawo." kwalla nashare nace "Naseem nace muku daddy zai dawo daddy yayi tafiya zai dawo." Nasmah tace "Mommy nikam kikaini gun Daddy kinji Mommy." kaina girgiza yayin da hawaye yake zuba a idona inajin yadda yaran suke bori Naseem yasaya yana fadin nikam ki kiramin Daddy, yami kamin wayata, yana ci gaba da faÉ—in na kira masa Daddy. kuka nafashe dashi na rungume yaran ajikina ina mai matuqar missing na Ahmad. Ummi ce tashigo ganin ina kuka tayi saurin isowa tana faÉ—in "HAMDAH lafiya?." kaina girgiza ina fadin "Ummi Ahmad yatafi bazan iya qiranshi a waya ba Ahmad yatafi kenan bazai dawo ba, bazan sake ganin sa ba, suma so suke su gansa." kuka sosai nafashe dashi Ummi ta rungume ni tana rarrashi na, kana tace na tashi nahaÉ—a kayana zamu tafi Bauchi tare, baza ta iya tafiya ta barni cikin halin da nake cikin nan ba. babu musu namiqe danni ma nasan tafiyar zai fi min bazan iya jure Ummi tatafi tabarni Anan ba. ita ta tai makamin mukashirya kayanmu tasa su Talatu suka fita dasu, gabadaya yan gidan suka rako mu parking lot, nace Mama ta komo part É—ina tun da ba kowa ciki kafin mu dawo, suna tsaye har muka shiga mota, muna É—agawa juna hannu muka fice a gidan. muka dauki Hanyar Bauchi... koda muka iso Bauchi naji daÉ—in ganina acikin yan'uwana domin kota'ina najuya sune basu kaunar ganin wata damuwa tattare da ni, kowa yana iya bakin kokarin sa wajen ganin farin ciki ya samu gare ni. Su Aunty Rafee'at da Aunty Jaleela kusan kullum sai sun zo gida sai dare su koma, Ya Mas'ud baya motsawa konan da can kullum muna tare idan ya dawo daga gurin ai kin sa, haka zai zauna muta hira. yan'uwana suna matuqar qoqari wajen ganin sun sani farin ciki sun kuma É—ebe min kewa... A hankali na fara sake wa, da muwar dake dankare cikin raina yana ta washe wa, yanzu kam alhmdllh na sake hankali na kuma nata kan daÉ—a kwanciya.. Zaune muke a parlour'n Mamie Aunty Rafee'at tafito daga kitchen rike da flaks da É—an madaidaicin tray mai É—auke da cup spoon da sugar, ta karaso cikin parluor'n, duba na tayi tana faÉ—in "Bari na kai masa na dawo." nace "Wa zaki kai masan Abbu ne?." tace "Ya SALEEM." kai na jinjina tare da faÉ—in "Anan kuma yanzu yake shan shayin sa yabaro gidan sa yazo nan ina matar tasa take?." baki Aunty Rafee'at ta taÉ“e tace "Ƴar wahala tana can asibiti kwance ita bata mutu ba batayi rai ba, tana kan karÉ“ar hukuncin ta." Ya Masa'ud yayi dariya da faÉ—in "Ai yanzu Ya SALEEM gauro ne tuni ya kaÉ—a matar tasa, yana gidan nan bashi da lafiya." shiru nayi ina jinjina lamarin a raina. Aunty Rafee'at ta fita domin kai masa shayin ta dawo muka ci gaba da hirar mu na tuna baya ana ta dariya, da tuna yaranta ta da da nayi ta yin sa, cikin muryar dariya Ya Masa'ud yace "Ƴar gidan Inna iyaye shirme." baki na washe nace "Allah Ya Masa'ud da ne nifa yanzu na girma." yace "Ah sosai ma kuwa dube ki fa kinfi na hannun dama nan nan girma yanzu." yayi maganar yana kallon Aunty Jaleela da ke gefen sa ta gefen ido. hararar sa tayi tana faÉ—in "Zamu sami matsala da kai Masa'ud ban son raini." nace "Ya Masa'ud baka sani ba jiya Uncle Habu da ya zo yace wai dama nice gaba da Aunty Jaleela ko." dariya duk muka yi cikin muryar dariya Aunty Rafee'at tace "Kai Masa'ud ka kiyayi kanka da haÉ—a rigima, ke kuma HAMDAH a ina Uncle Habun ya faÉ—i haka?." dariya nayi nace "Ai ita tasan lokacin." fuska Aunty Jaleela ta haÉ—e tana hararar mu tare da faÉ—in "Ni ba sa'ar ki bace daga ke har Masa'ud É—in." "To gyanbo duk kin girme mu kice har da Aunty Rafee'at É—in ma ke har da ma Ya SALEEM, wlh yanzu yasa na kai masa bulalar zane ki, ni kuma nace ya huta tun da bashi da lafiya yana zaune na tsumage ki." kafaÉ—ar sa Aunty Rafee'at ta buga tace "Tashi ka bar nan tafi damuwar ka." ya mike yana dariya yafita. Aunty Jaleela ta É—aga murya tana faÉ—in "Yan zu ma zaka iya É—auko bulalar." Bayan sallar Isha mazajen su Aunty Rafee'at suka zo É—au kar su, har gurin mota na rako su, Ya SALEEM na hango zaune kan kujera Dr Farooq na zaune kusa da shi, tun da nazo gidan sai yau na saka shi a ido na, ban ma san yana gidan ba sai É—azu da su Aunty Rafee'at suke faÉ—a, kai na na kawar daga kallon sa na mai da hankali na kan su Aunty Rafee'at. Dr Farooq yaÉ—an É“ata lokaci a gurin sa ga dukkan alamu duba shi yake game da rashin lafiyar sa da aka faÉ—a, dan har su Aunty Jaleela suka tafi yana gurin sa, sai can ya mike ya taho in da muke suka shige mota ina yi musu sai da safe, Dr Farooq yace "Ƴar gidan Inna yaushe zaki zo mana?." nace "Kuna zaune zaku ganni." dariya yayi da faÉ—in "Babu rana kenan ko da shike manya fitar su na da wuya sai dai a zo musu basu suzo ba." "Akwai rana kai idan tazo shine zaku gannin ai." yace to Allah yasa... ina tsaye har suka fita. a hankali na juyo zan ko ma ciki, Ya Masa'ud ya fito rike da Hannun su Nasmah, suna ta zuba masa surutu, in da Ya SALEEM yake suka isa, murmushi mai sanyi ya sake ganin yaran ya miko hannu yana kokarin ruko hannun su, murya na É—aga nace "Naseem Nasmah kuzo nan muje ku kwanta." cak ya tsaida hannunsa kana ya É—ago a hankali ya kalli in da nake, da hannu na kuma yi musu alama da su taho ina ci gaba da faÉ—in "Ku wuce muje ku kwanta nace." suka juyo suka taho in ds nake na ruko hannun su muka wuce sashin Ummi... Washegari da safe duk muna side É—in Mamie Ya Masa'ud ne kawai baya nan yatafi gurin aiki. waya ta dake gefe na su Naseem suka É—auka wai sam sai na cire musu a key sun yi game, sai da na cire musu kafin suka dai na fitina ta. can anjima sai ganin su nayi sun shigo daga waje, nace "Ku ina waya ta?." Nasmah tace " Na guyin Uncle." nace "Wani Uncle É—in?." tace "Uncle É—ayan." "Wani Uncle É—ayan yaushe Ya Masa'ud É—in ya dawo daga gurin aiki." Naseem yace "Ba yace shi Daddy ne ba Uncle ba." yayi maganar ysna rike haÉ“a da ware idanu. Nasmah ta gyaÉ—a kai tare da faÉ—in "Eh yana guyin Daddy." da sauri cikin É—aga murya nace "Ku rufa min baki shi ba Daddyn ku bane Daddy'n ku ya rasu." cikin tsawa Ummi tace "Ke HAMDAH baki da hankali ne kin san me kike faÉ—a kuwa, wani irin tarbiyya kike son basu, to wannan shine uban su na asali shi da kike faÉ—an ubansu uban su ba ubansu bane uban arone, baki da ta in da zakiyi ki sauya musu uba." Mamie tace "A'a Ummin Fauzan wai ke laifin ta kike gani ne, sam bata da laifi kuma bata faÉ—i karya ba, Ahmad yayi musu abun da shi ya kasa iya yi musu a matsayin sa na uban nasu ai shi ya kamata a kira sa da uban aro, basu san shi ba Ahmad suka sani a matsayin uba kuma har gobe zasu cigaba da ganin sa a matsayin uba, tun da shi ya gaza a cikin rayuwar su." mikewa nayi na nufi kofa na fita. can na hango shi zaune in da jiya na gansa yana zaune kan kujera ya É—aura kafafunsa kan wata kujerar dake gaban sa, idanunsa a lumshe ya naÉ—e hannayen sa a kirji yayin da bayan ke jin gine jikin kujerar. har na nufi sashin Ummi najiyo karar waya ta, da É—an sauri na juyo, sai naji karar daga inda yake yake fitowa, kiran ya katse wani ya kuma shigowa, nasan me kiran bai wuce manajan gidan mai na ba dan É—azu mun fara magana da shi bamu gama ba. a hankali na juyo na nufi inda yake jin wani kiran ya kuma shigo wa a karo na huÉ—u, a sannu na iso in da yake daidai lokacin wani kiran yakuma shigowa, kallon inda sautin wayar tawa ke fitowa nayi, sai ganin wayar nayi a cikin kirjin sa ya rungume shi har lokacin idanunsa a nufe. kai na naÉ—an kawar daga kallon sa kana na mika hannu jin wani kiran ya kuma shigo wa, ina kokarin zaro wayar dags kirjin sa. a hankali ya buÉ—e lumsassun idanunsa ya zuba su a fuska ta yayin da idanun mu ya sarkafu dana juna, da sauri na janje idanuna daga nashi kana nayi hanzarin zare waya ta da ga kirjin sa, na juya da sauri jin zuciya ta yana wani irin tsalle haÉ—e da bugawa, su Naseem na gani sun fito daga side É—in Mamie da sauri naje na ruko hannun su na janyo su muka shige side É—in Ummi. tun daga ranar ban sake barin su sufita ba bare su haÉ—u da shi, idan ina side É—in Mamie ne ma to muna tare da su bana taÉ“a barin su su matsa ko nan da can, bare ma su fita ya gansu har suje in da yake. niko tun da na zo gidan gaisuwa bai taÉ“a haÉ—a ni da shi ba bare maganar baki... bayan wata É—aya Zaune nake a parlour'n Ummi muna hira na waiga gefe da gefe na banga su Nasmah ba, da sauri na mike nashige bedroom É—in Ummi nan ma basa nan da sauri nafita na yi waje ina kiran sunan su, can na hango su rike a hannun Ya SALEEM sun fito daga side É—in Mamie sun nufi get, da sauri na biyo bayan su ina isa in da suke da sauri na ruko hannayen su ina faÉ—in "Ku wuce mu tafi." juyo wa yayi batare da yasaki hannayen su ba yaÉ—an zuba min lumsassun idanunsa, yana bina da wani irin kallo tamkar yau ya fara sani na, niko hannun su nashiga ja ganin bashi da niyyar sakin su, yana rike da su gam niko sai daÉ—a jan su nake, a hatsale cikin kunar rai da tuno a bin da yayi min a baya nace "Sake min yara ina zaka kaimin su." nayi maganar cikin bushewar zuciya, da mamaki yake kallo na nasan mamakin yadda na iya tsayuwa nake gaya masa magana babu shakka ko tsoro yake, niko a yanda nake jin zuciya ta zan iya gaya masa fiye da haka danni yanzu bana jin tsoro ko shakkar sa, baki ya motsa kana ya soma magana kamar mai jin bacci "Idan kika ji musu rauni sai nayi maganin ki, sakar musu hannu." zan tafi da Æ´aÆ´a na bazaki sake ganin su ba, bare kicigaba da nisantasu gare ni." da sauri nace "Su ba Æ´aÆ´an ka kane ban kuma yarje maka kafita min da su ko nan da kofar gida ba, babu in da zaka je min da su, ka sakar min Æ´aÆ´a na." nayi maganar ina mai daÉ—a jan su. da sauri ya saki hannun su tare da fizgo ni ya har sai da na garu da jikin sa, yarike hannaye na gam a hankali cikin yanayin nan nasa ya soma magana yayin da sautin maganar tasa ke fita da É—an sautin numfashi irin na mara lafiya, "ƳaÆ´a na ne idan kika kara nesan tani gare su." ya taune lips É—in sa tare da girgiza kansa. kokarin kwace kaina mashiga yi ins faÉ—in "Su ba Æ´aÆ´an ka bane ba kuma zasu taÉ“a zamowa naka ba." maganar Mamie mukaji a bayan mu tana faÉ—in "Sake ta ai ba karya ta faÉ—a ba, kai da kan ka kafaÉ—i cewa su ba naka bane tun suna ciki ba'a gama yi musu halitta ba, baka kuma isa yanzu kadawo kace naka ba ne, sake ta maza." sake ni yayi ya juyo in da Mamie take kamar zaiyi magana miskilancin nasa ya hana shi iya cewa komai, sai dai bugun zuciyar sa daya karo. da sauri na ja hannun su Nasmah muka wuce ciki... ina shiga na soma haÉ—a kaya na, koda Ummi ta shigo taga ina haÉ—a kaya ta tanbaye ni, nace mata gobe zan tafi ana nema na game da harkoki na da gaggawa, washegari kuwa da sassafe nabar garin Bauchi..........! 8/19/22, 11:01 - Ummi Tandama😇: 38 Sai da na dawo Abuja kafin hankali na ya kwanta nayi masa nisa da yaran bazai sake ganin su ba bare ya sami bakin faÉ—in cewa su Æ´aÆ´an sa ne. yanzu harkoki na da na Ahmad karami kaÉ—ai nasa a gaba, duk da ko mai bai canza ba ma'aikatan da suke ai ki karkashin Ahmad su suka cigaba da gudanar da aikin a karkashi na. Bayan wani lokaci sabuwar rayuwa na gina wa kaina, abisa rashin Ahmad na nutsar da zuciya ta na fauwala wa Allah komai na rungume kaddar rashin sa, idan na tuno da shi da rayuwar da mukayi dashi wani lokaci na zauna nayi kuka wani lokaci nayi dariya, sannan nayi masa addu'a, nakuma sawa raina nagama aure kenan a duniya bazan kuma maimaita kuka na uku a cikin aure ba, kamar yadda nayi a baya, da farko nayi kukan kazafi da wahalar rayuwa dalilin auren Ya SALEEM, daga bisa ni nayi kukan rabuwa da Ahmad a lokacin da na yi sabo da shi, yanzu kam zanyi rayuwa ta ce cikin salama ni kaÉ—ai sai Æ´aÆ´a na...👌🻠A gajiye na dawo gida daga gurin mittin É—in da muka gudanar yau da ma'aikata na, a parlur na tadda Mama goye da Ahmad, "Mama barka da gida Ahmad É—in ne goye a baya har yanzu zai sa miki ciwon baya fa." nayi maganar ina zama kan kujera, Mama tayi murmushi tare da faÉ—in "To ya zanyi tun da ai kin aure nake, ai wannan angon shi maganin sa goyo idan ba haka ba yarika haÉ—a kashi kenan da kiriniyar sa, É—azu wai shi zai sauko kasa da kansa kaÉ—an ya rage yayi dungure." dariya nayi nace "Tab da yau keya yasha kasa kenan." tace "Ai kuwa." Talatu ce tashigo parlour rike da da tray mai É—auke da kayan motsa baki ciki, ta dire shi kan table wÉ—in gabana tanayi min sannu da dawowa, na amsa tare da yi mata sannu da aiki. na gyara na soma cin abin da ta kawo min. waya ta ce tayi kara murmushi nayi ganin Aunty Rafee'at ce ke kiran na É—aga tare da yin sallama, ta amsa jin yanayin muryar ta sauri nace "Aunty Rafee'at lafiya ya naji muryar ki haka?." tace "HAMDAH Ya SALEEM bashi da lafiya muna asibiti ne jikin sa ya tashi sosai." É—an shiru nayi jin yanda take maganar kamar zatayi kuka cikin rauni sosai. nace "To ikon Allah jikin har haka ne to Allah ya sawaka." bata kuma iya cewa komai ba sai kashe wayar tayi, fuska na yamutsa a kasan raina nace "Fatan saukin ma dana maka albarkacin Æ´an'uwan taka ce." A can sashin su Bappa kiran Abba ne ya shigo wayar Bappa bayan sun gaisa, Abba ke sanar masa da SALEEM ba lafiya sosai yana asibiti. hankalin Bappa yatashi sosai dajin lamarin, lallai ciwon babba ne tun da har aka kwantar da SALEEM a asibiti. yace gobe yana zuwa insha Allah, washegari da safe Bappa ya É—au hanyar Bauchi. koda ya isa asibitin da aka kai SALEEM yasa aka kai shi, hankali sa ya tashi matuka ganin halin da SALEEM yake, yana kwance baya ko motsi na'urori suna ai ki a jikin sa. cikin matukar tashin hankali Bappa yake tambayar su Abbu me ya ke damun shi me likita yafaÉ—a game da ciwon nasa. Dr Farooq ne ya shigo da wasu likitoci su huÉ—u suka dukufa a kansa kowa da kalar gwajin da yake masa, Dr Farooq yaÉ—an yi baya tare da faÉ—in "Ya salam." a cikin zuciyarsa, ya juyo ya kalli su Abba da Abbu da Bappa dasuke tsaye jungum-jungum, kansa ya kawar ganin sun kura masa ido suna so suji ta bakin sa. É—aya daga cikin Doctors É—in ne ya É—ago tare da share zufa ya kalli sauran Æ´an'uwan sa sukayi magana sakanin su kana ya juyo gasu Abbu yace "Kuyi Hakuri a gaskiya yana cikin hatsari sosai zuciyarsa sa yana daf da bugawa, amma zamuyi iya bakin kokarin mu daga nan zuwa kwana biyu har idan ba'a sami wani sauyi ba, to gaskiya sai dai a É—aga shi a kasar nan a cikin kwana kin nan." salati Bappa ya sake hankali tashe yake faÉ—in "Bugun zuciya kuma Innalillahi wa'inna'ilaihirraji'un, garin yaya akayi haka yau she yafara ciwon zuciya da har zuciyar ke kokarin bugawa?." Dr Farooq ya gyara tsayuwar sa yayin da likitocin suka fita, Bappa ya matso jikin gadon da SALEEM ke kwance idanunsa a rufe yayin da yake fidda numfashi É—aya na bin É—aya, Bappa ya dubi su Abbu yace "Tun yaushe yake cikin wannan halin kuma mene ne musabbabin sa?." Dr Farooq ne yace "Tun ranar da HAMDAH ta bayyana tafiyar ta na wannan karon kuma shi ya haifo da wannan babban matsalar, kuyi hakuri tun wancan lokaci ban sanar wa kowa bane sabo da ina sa ran zai iya samin sauki ta hanyar shan magani da kuma rage tunani, sai dai a yanzu komai ya kwaÉ“e kuma na lura da tun ranar da HAMDAH tabar garin nan washegari dana kuma yi masa gwaji sai naga ciwon nasa ya É—are na da, sai dai abin da na lura baya amfani da shawarwarin da na É—aura shi a kai yawan tunani da kuma damuwa shi ya janyo sa izuwa wannan matakin." da mamaki su Abbu suke jin maganar su sam basu taÉ“a sammanin haka ba, Bappa ko kai ya jinjina yana mai cigaba da kallon SALEEM dake kwance numfashin sa yana sama yana kasa. Dr Farooq yace "Sakamakon allurar da akayi masa shi yasa yasami baccin nan, zamu jira zuwa ya farka muga abin da ya dace, zamu É—an bashi guri yasa mi baccin da kyau." duk suka fita a É—akin domin barin sa ya sami baccin... Bayan wasu É—an awanni ya farka daga baccin da yake, sai dai har yanzu babu abun da ya sauya daga halin da yake ciki, bayan likitoci sun shiga sun daÉ—a dudduba shi suka fito, Dr Farooq yace wa su Abbu zasu iya shiga su gansa yanzu, yana kwance har lokacin amma idanunsa a buÉ—e suke yanzu, sai dai babu in da yake na'urori ne ta ko ina ke ai ki a jikin sa. suka karaso in da yake suna yi masa sannu, Bappa yace "Sannu SALEEM ya jikin?." kwayar idanunsa kaÉ—ai ya juya ya É—an kalli Bappa kana ya É—an lumshe su tare da buÉ—e su a lokaci guda, Bappa ya gyara tsayuwar sa da kyau ya kalli sa kana yace "Akan wani dalili kake son salwantar da rayuwar ka, kunshe damuwa cikin rai mai cutar wa bazai taÉ“a haifar da maslaha ba, ka dubi halin da ka jefa kan ka ciki, muma ka jefa mu. SALEEM kana son komawar auren ka da Æ´ar'uwan ka, a kan hakan kake son salwantar da rayuwar ka ta hanyar É“oye hakan acikin zuciyar ka." "SALEEM." Bappa yakuma kiran sunan sa, kana yace "Kana son komawar auren ku da HAMDAH?." shiru yayi tare da yin kasa da idanunsa yana wani taune leps É—in sa, Bappa yakuma faÉ—in "SALEEM kana son mai da matar ka?." nan ma bayyi magana ba sai É—ago idanunsa da yayi ya kuma kallon Bappa, yayin da bugun zuciyarsa ya karo, Bappa yagirgiza kai tare da yin murmushi irin nasu na manya kana yace "Miskili kafi mahaukashi ban haushi, to ka faÉ—awa zuciyar ka ta sami nutsuwa za'a bata abin da take so, basai tayi bindiga ta fashe ba." idanunsa ya lumshe tare da jan numfashi mai É—an tsawo a bayyane, a hankali ya É—ago hannusa izuwa kan kirjin sa ya kife tafin hannunsa kan kirjin nasa dake harbawa da sauri-sauri. Abbu yace "Bappa shin ka mance abin da ya mata ne kayi hakuri da abin da zan faÉ—a Bappa, idan aka mata haka sam ba'a kyauta mata ba, kada mu kuma maimaita kuskuren baya, ya kuma cutar da rayuwar ta, sam bai cancance ta ba." Abba yace "Hukun cin da Bappa ya yanke shine kaÉ—ai mafita, shin zamu cigaba da zuba ido ne muna ganin sa cikin halin mutuwa ko rayuwa." Bappa yayi waje su Abbu suka bi bayan sa, koda suka fita Bappa ya dube Abbu kana yace "Ka sani SALEEM bashi da laifi duk abun da ya faru sharrin ma sharranta ne." Abbu yace "Da kuma halin sa, in da sharrin wasu har da ma halinsa, kada mu shiga hakkin yarinyar nan." "Kada ku kuma cewa komai a kan gamanar nan na gama yanke hukunci." Bappa ya faÉ—a yana tafiya hanyar masallaci dake cikin asibitin." bayan kwana biyu da tafiyan Bappa dasassafe yaqirani yace nazo Bauchi yanason ganina da gaggawa, natsorata dajin qiran da Bappa yamin na gaggawa sai naqira wayan Ummi danjin mekefaruwa naji wayar Ummi akashe, jin wayar Ummina akashe Hankalina yayi mummunar tashi atake nazari mayafina naja yarana mukayi waje tunkafin na isa parking space nake qiran Driver, ya iso da gaggawa nace masa maza yanzu mutafi Bauchi, yana tambayar lafiya hajiya ban saurareshi ba na saka su Naseem cikin mota kawai nima nashiga. nace masa tafiya mai sauri zamuyi ba É“ata lokaci yaja motar, cikin awa huÉ—u da rabi muka iso cikin garin Bauchi saboda gudun da driver yake shararawa. koda muka iso gida hankalina yayi mugun tashi ganin babu Kowa a gidan numbern Bappa naqira nace Bappa "Na iso ina mutanen gidan?." yace kizo asibitin Dr Farouq gamunan anan, dasauri nafita nashiga motan piiiiiiiii naja motan ko Driver bantsaya qiraba bantsaya ko ina ba sai asibitin. ina daidaita parking natsaya su Naseem suka biyoni dasauri ina shiga cikin asibin naga mami da Ummi Aunty jaleela Aunty Rafee'a Fauzan Ya Mas'ud suna gani na suka mike duka suna faÉ—in "Zuwan yau she kenan?." murmushi nayi kana na karaso in da suke, na dube su ina faÉ—in "Ina su Abbu da Abba ina Bappa?." Ummi tace "Suna cikin É—aki in da aka kwantar da SALEEM." numfashin mai karfi na sauke jin kowa yana lafiya, nace "Kai wlh har hankali na ya kwanta na É—auka wani mummunar abune ya faru ashe dai kowa lafiya." Ummi tace "Eh to gamu nan dai kowa lafiya amma SALEEM gashi can a kwance babu in da yake." baki na taÉ“e tare da faÉ—in "Allah ya sawaka." na juya ina kukarin zama kan kujera, Ummi ta ce "Baki shiga kin duba shi ba kike kokarin zama a nan, je ki duba shi kafin ki zauna." fuska na É—an yamutsa tare da mike wa na nufi kofar da take nuna min. da sallama na tura kofar, su Abbu suna tsastsaye suka amsa min sallamar, idaduna ne ya sauka kan gadon dake cikin room É—in Ya SALEEM na kwance idanunsa a lumshe numfashin sa yana sama da kasa na'urori suna ta ai ki a jikin sa. a hankali na karaso cikin É—akin. tare da soma gaida su Abba, suka amsa suna yi min sannu da hanya. Bappa yace "Kin iso?." nace "Eh na iso." yace "To madalla." ya dube Ya SALEEM da ke kwance tare da duba na yace "Kiyi masa sannu da jiki." naÉ—an dube shi tare da faÉ—in "Ya jiki?." idanunsa ne suka motsa daga lumshen da suke a hankali yashiga kokarin buÉ—e su, har ya ida buÉ—e su a kai na. a yanayin da yake ciki bana sa ran zai iya amsa ya jikin da na masa dan gaba É—aya yagama fita hayyacin sa, kai na na kawar daga gare sa, a hankali ya mai da idanunsa ya kuma lumshe su tare da sauke numfashi mai sauti. Bappa ya dube ni tare da faÉ—in "Zo nan HAMDAH ina da magana da ke." yayi maganar yana juyawa tare da fita a É—akin. nabi bayan sa muka fita can farfajiyar asibitin, gefe muka samu Bappa ya zauna kan dakali lima na zauna gefen sa. ya dube ni da kyau yana faÉ—in "Kun zu lafiya dai ko ya hanya?." nace "Lafiya lau." yace "To madalla." zaman sa yaÉ—an gyara kana yace "HAMDAH." ya jira suna na, na juyo gare sa tare da amsa kiran nasa. yace "Mene ne matsayi na a gare ki?." É—an jim nayi dajin maganar nasa kana nace "Ko a da da bansan kai waye a gare ni ba, matsayin uba nake ganin ka bare yanzu da ya kasan ce kai É—in uba ne kuma kaka a gare ni." yace "Madalla naji daÉ—in jin hakan ina kuma alfahari da ke, da biyayyar ki nasan bazaki taÉ“a bani kunya ba, HAMDAH ina son ki sani yau na mayar da auren ki da É—an uwan ki." wani irin dadammm kirjina ya buga da mugun karfi, na wani irin mike wa a razane a kuma zabure, ina bin Bappa da wani irin kallo. Bappa ya ruko hannuna tare da maidani zaune, yace "Ki nutsu kiji abin da zan faÉ—a miki, É—an uwan ki yana cikin mawuyacin hali halin mutuwa ko rayuwa, kuma duk a ta sana diyyar ki ne, kin ganshi kuma kin ga halin da yake ciki, ke kaÉ—ai zaki iya tsamo shi daga cikin halakar dayake dumfaro shi na bugawar zuciya, likitoci sun bamu tambacin har idan yau yagaza samin abinda yake muradi a ciki. zuciyar sa to ba shakka zuciyarsa zata iya bugawa ya mutu, ke yake muradi a zuciyarsa sabo da gudun kada mu rasashi shi yasa na mai da auren ku da shi yau, nasan wannan hanyar ce kaÉ—ai zai iya kuÉ“utar dashi daga cikin halin da yake." kai na shiga girgiza wa ina faÉ—in "Sam bani ce cikin zuciyarsa ba, Bappa Ya SALEEM ya tsane ni baya kauna ta Bappa me yasa zaka mai da ni cikin halaka rayuwa da shi tamkar halaka ce, ina murnar rayuwa ta tasami salama ashe dai a cikin kunci da wuya zan tabbata, Bappa bana son komawar auren nan dan Allah ka raba auren nikuma zanyi nesa da ku bazaku sake gani na ba tun da bakwa son ganin farin ciki na, aure na da Ya SALEEM tamkar rugujewar farin ciki nane, wata a zabar zan kuma fuskanta ta sanadiyyar sa a karo na biyu." kuka ne nafashe da shi tare da haÉ—e hannaye na ina faÉ—in "Dan Allah dan Allah Bappa karaba auren nan wlh bana so." numfashi Bappa ya sauke kana yace "Kiyi hakuri ki ceci É—an uwan ki kada ki bari ta sana diyyar ki ya mutu, babu abun da zai faru da rayuwar ki Allah bazai bawa azzalumai masara tsoron Allah nasara a kan ki ba, É—an uwan ki na bukan ki ke da Æ´an shi." kai narika girgiza wa ina faÉ—in "A'a a'a Bappa dan Allah, ba Æ´aÆ´an sa bane su ba Æ´aÆ´an sa bane." na mike zumbur da sauri naje na ruko hannun su Naseem na jasu da sauri nanufi mota, muka shiga muka bar asibitin... Motar Bappa yabi da kallo kana ya mike yashiga ciki, a bakin kofar É—akin da SALEEM ke ciki ya haÉ—u da su Abbu har da su Mamie suna tsaye kowa yayi jungun-jungun, jiki a sanyaye Bappa ya iso in da suke yana faÉ—in "Ya'ya lafiya?." Abba yace "Ina HAMDAH take...... 8/19/22, 11:01 - Ummi Tandama😇: 39 Bappa yace "Ta tafi bata tsaya ta saurare ni ba, bata kuma taÉ“a yimin haka ba, HAMDAH, bata taÉ“a ketare magana ta ba, hakika tana cikin tsoro da tuno rayuwar ta ta baya tana tsoron kada ta kuma shiga halin da ta shiga a baya." cikin rawar murya da zubda kwalla Ya Mas'ud yace "Bappa numfashin Ya SALEEM yana kokarin barin jikin sa." salati Bappa yayi da sauri ya shige cikin É—akin in da likitoti suke tsaye ca a kansa. tuni kowa ya fara kwalla su Aunty Rafee'at har da jan shassheka, Mamie tayi baya duk daure zuciyar ta da take sai da hawaye suka zubo mata, ta zauna a gefe tana mai cigaba da zubda kwalla. da sauri Ummi ta nufi kofar fita tayi waje, direba ta saka ya kaita gida da sauri tana isa, direct sashin ta ta wuce tun daga parlour take jiyo shesshekar kuka, da sauri ta karasa cikin bedroom. ina zaune cikin É—akin nahaÉ—a kai da guiwa sai rusar kuka nake, a sannu ta karaso kusa da ni ta zauna gefe, a hankali ta dafa kafaÉ—a ta tare da kiran suna na tace "HAMDAH na tabbata kinsan kuna da É—acin rabuwa irin na mutuwa, HAMDAH ga uwa can tana kukan rabuwa da É—an ta da yake kokarin barin duniya a ta sanadiyyar ki, shin bazaki zamo mai yafiya a rayuwa ba, shin kin san falala da tarin lada a gun duk wan da ya ceci wani daga faÉ—a wa wata halaka, É—an uwan ki ne fa shi shin ashe bazaki zamo mai share mana hawaye ba, ni mahaifiyar ki ina mai rokon ki da kije ki ceci É—an uwan ki, ba zanyi miki dole ba amma ki sani har idan SALEEM ya mutu duk ahali zamu rataya miki alhakin mutuwar sa a kanki, sannan baza mu taÉ“a dai na ganin ki a matsayin wan da takasa taimakon ahalin ta ba." Ummi ta mike tana sharar kwalla ta nufi kofa zata fita, da gudu na mike naje na ruko hannun Ummi, cikin muryar kuka nace "Ummi na kiyi hakuri kar kuyi fushi da ni Ummi ina jin tsoro ina jin tsoro ne." kai ta girgiza min tare da share min hawaye ta ruko hannuna gam-gam cike da karfafa guiwa tace "Babu abun da zai faru da yardar Allah kisawa zuciyar ki hakan, zamu tsaya miki da karfin ikon Ubangiji babu abin da zai kuma faruwa." kai nashiga gyaÉ—a wa alamun gamsuwa yayin da hawaye ke ci gaba da zuba a ido na. ta janyo hannuna ta haÉ—o da na su Naseem muka fita. koda muka iso asibitin hannuna Ummi ta kuma ruko wa tana É—auke da Ahmad karami Naseem da Nasmah suna gaban mu, muka shiga asibitin. su Mamie da Aunty Rafee'at Aunty Jaleela Nusaiba Fauza suna tsastsaye a bakin kofar É—akin da Ya SALEEM yake ko wannen su kuka yake da hawayen sa, jiki a sanyaye muka karaso in da suke, hankali tashe Ummi ke tambayar su lafiya. cikin zubda kwalla Aunty Jaleela tace "Ummi Ya SALEEM baya numfashi." tuni hawaye yafara zuba a idanun Ummi, niko jiki na ne ya É—au ki É“ari, Ummi ta kuma ruko ni gam ta janyo ni muka shige cikin É—aki. doctors ne ke tsaye a kansa suna ta fafutukar ceto numfashin sa, Bappa Abba Abbu Ya Mas'ud suna tsaye a gefe. Bappa sai anbaton sunan Allah yake Ya Mas'ud ko sai sharar kwalla yake, lokaci zuwa lokaci Abba ke kai hannunsa karkashin idanunsa yana share É—an guntun kwallar dake fito masa, a É“angaren Abbu ma haka. É“arin jiki na ne ya karu lokacin da idanuna ya sauka kan Ya SALEEM dake kwance ko matsi baya yi babu alamun numfashi tattare da shi, sosai jiki na ke kakkarwa, zuciya ta tayi rauni tausayi mai haÉ—e da kawa zucin É—an uwa suka lulluÉ“e ni, ko ba komai Ya SALEEM jina na ne dole naji makamancin hakan a tattare da ni, domin É—an uwa yawuci wasa koda ace kuwa a kullum yana kuntatawa rayuwar ka, ka gansa a gaban ka tamkar mutacce dole zuciyar ka ta girgiza. da sauri na fizge hannuna da gudu na fasa sakanin doctors É—in na faÉ—a a jikin sa tare da girgiza shi ina faÉ—in "Ya SALEEM kar ka mutu ka tashi dan Allah ka tashi kar ka mutu Ya SALEEM Ya SALEEM Ya SALEEM". na karasa da kiran sunan sa da karfi ina mai jijjiga shi. tuni Naseem da Nasmah suka saki kuka suna kiran Daddy Daddy. sosai nake gargiza shi ina kiran sunan sa yayin da nake rusa kuka mai karfi, a raina ina ayyana shike nan babban yayan mu ya tafi ya barmu, duk miskilancin halin sa da rashin dariyar sa muna son sa a haka, ga Æ´an uwa na da mahaifiyar sa tana kukan rashin sa, hakika rashin wani naka na da zafi, shike nan shima ya tafi bazai dawo ba, kamar yadda Inna da Ahmad suka tafi tafiyar da babu dawowa.. wani kuka ne nakuma sake wa da karfi ina faÉ—in "Ya SALEEM kai kar ka tafi dan Allah kada ka tafi ka barmu ka tashi Ya SALEEM ka tashi." nayi maganar ina mai girgiza shi da karfi. fuska ta na kife cikin kirjin sa ina jujjuya fuskar tawa da gogashi cikin kirjin nasa ina mai ci gaba da kukan. a sannu ya sauke wani irin numfashi mai tsawo kana yashiga motsi da idanunsa. cikin matukar mamaki likitotin ke kallon ikon Allah, mutumin da numfashin sa ya tafi bugun a gogon hannun sa ne kaÉ—ai yake iya tabbatar musu da yana raye shima bugun hannun nasa yana daf da tafi dan sai ya É—au tsawon mintina masu dama kafin ya É—an buga sai ka lura sosai kafin ga gane hakan shima, da sauri su Bappa suka maso suna mai mamakin hakan suma, dan gaba É—aya sun gama cire rai da shi suna jiran jin ta bakin likitotin kawai. da sauri na É—ago kai na jin yana motsa jikin sa na kurawa fuskar sa iso, ganin idanunsa suna motsi a lamar yana son buÉ—e su. da sauri nace "Ya SAKEEM buÉ—e idanun ka Ya SALEEM ka buÉ—e ka huÉ—e kada ka tafi ka harmu." a hankali yashiga buÉ—e idanun nasa har ya ida buÉ—e su a kan fuska ta, a sannu ya É—ago hannunsa ya sauke sa kan nawa ya rike shi gam, a hankali ya juya fuskarsa in da su Naseem suke yayi musu alama da hannu da suzo in da yake, suka matso bakin gadon suka kwantar da kansu a jikin sa, numfashi mai sauti ya sauke yana mai daÉ—a damke hannuna tare da shafa kan yaran da hannunsa guda. gaba ki É—aya Æ´an cikin É—akin farin ciki ne bayyane a kan fuskokin su, hatta likitotin, É—aya daga cikin Dr ya dube ni da murmushi yace "Sannu da taya mu ai kin da ke kokarin gagarar mu." "Itace maganin ai." É—aya Dr dake kusa da shi ya faÉ—a yana É—an dariya... Ya Mas'ud yafita da sauri sai gashi da su Mamie sun shigo har suna rige-rigen shigo wa. fuskar Mamie É—auke da murmushi mai bayyana tsantsar farin cikin ganin sa ya farfaÉ—o daga sammanin mutuwar da suka saka masa. kowa sai sannu yake masa, sai dai babu wan da ya amsa shi, hakan bai dami kowa ba dan kowa yasan hakan halin sa ne. hannu na dake cikin nasa na É—an motsa ina kokarin janye hannun nawa, dan irin kallon da yake min yasa ni jin wani iri cikin jikina, ga kuma idanun kowa a kanmu. gam yada É—a rike hannun nawa bai kuma fasa bina da irin wannan kallon ba. Aunty Rafee'at da bakin ta ya kasa rufuwa dan murna ta juyo ta kalli mijin ta Dr Farouq, shima murmushi yayi tare da É—an dungurin ta cikin kasa da murya ya ce "Kin ga yayan ki ko so nason kashe shi ga kallon da yake mata kamar bashi bane É—azu ke kokarin mutuwa." hararar wasa tayi masa tace "To an faÉ—a maka so karya ne." yace "Ni zan bada shaida ba karya bace gashi ina kan fama da shi a kan ki." ya karasa maganar da kashe mata ido, dariya tayi tana ture kafaÉ—ar sa... Hannu na na zare cikin nasa da É—an sauri cikin jin kunya ganin su Abbu sun matso kusa da shi suna yi masa sannu, shiko idanunsa na kaina, yana yi min wani irin kallon cikin ido. baya nayi ina mai jin kunya. bayan wasu É—an mintina likitoti sukace a É—an bashi guri ya huta bayan sun masa allurai... a ranan da yamma Ya SALEEM yace shi zai koma gida, Dr Farooq yace ya bari ya daÉ—a jin kwarin jikin sa, yace shi sam zai tafi dan shi lafiyar sa lau, sai da su Bappa suka sa baki kafin da kyar ya yarda. kwanan sa uku a asibitin kullum a can muke wuni dukan mu, idan na shiga É—akin yi masa sannu da jiki haka zai kafe ni da ido yata kallo na kamar bai taÉ“a sani na ba. su Nasmah kam ko da yaushe suna jikin sa, sai dare idan zamu koma gida suke rabuwa da shi. ranar da ya cika kwana huÉ—u yace bazai kuma kara kwana cikin asibitin ba, dun dole a ka bashi sallama. nuka koma gida kowa hankalin sa kwance da farin cikin samun lafiyar sa..... A ranar Abbu ya sa a ka kirawo ma'aikatan gidan Ya SALEEM dukan su waÉ—an da suka yi aiki lokacin ina gidan, wato waÉ—an da suka bada shaida kan sunga wani yana zuwa guri na lokacin da Ya SALEEM yayi tafiya. dukkan mu a parlour'n Mamie muka haÉ—u,har da Ya SALEEM da Abbu yayi masa dole yabaro É—akin sa na cikin gidan yazo gurin taron. ganin ma'aikatan ya sani tuno wa da abunda ya faru a baya sai nake ganin kamar yau hakan ta faru. bayan addu'a da Bappa yayi Abbu yayi gyaran murya kana ya dubi ma'aikatan É—aya ba yan É—aya, Baba Mai gadi Sani direba Habu mai shara sai Salele wan da shi a lokacin bai bada shaidar ba sai dai kasan cewar yana aiki a lokacin yasa shima a ka gayyato shi. Abbu ya dube su da kyau yace "A wancan lokacin kunyi kokarin bata mana family kuka kuma yi sana diyyar raba aure da tarwatsa mana family, dukkan ku bazan kyale kowa ba zan É—au mataki a kanku zakuyi bayani a gaban kotu, har da kai da girman ka mai gadi baka ji kunyar bada shaidar karya ba." baba mai gadi yashiga jan hanci da matsar kwalla yana faÉ—in "Allah ya huci zuciyar ka Alhaji ayi hakuri wlh sharrin shaiÉ—an ne, amma da fari na ki karÉ“ar kuÉ—in da Hajiya ta bamu kan muyi shaidar, tace har idan bamu yi abun da tace to to abakin aikin mu shine naji tsoro na karÉ“i kuÉ—in, amma wlh duk abun da ya faru karya ne Hajiya ce ta shirya komai tace mu faÉ—a." Bappa yayi salati yace "Akan kuÉ—i akan kuÉ—i kuka tarwasa aure kuka jefa yarinya cikin ukubar rayuwa Allah bazai kyale ku ba." Salele yace "Wlh Alhaji lokacin can data bani kuÉ—i kan nayi shai da naki sai tace har idan na faÉ—a sai tayi min sharrin da bana sammani, sai tace har dani ta taÉ“a kama ni É—akin Hajiya HAMDAH shi yasa naji tsoro ban faÉ—a ba." Abbu yace "Yanzu kam komai ya zo karshe ita wacce ta shirya muku makircin bagata can kwance a asibiti Allah ya fara nuna mata iyakar ta ba, ai ba ayi wa Allah dabara, kukuma mai gadi da Habu da Sani yau za'a kurfanar daku gaban Shari'a kotu zata yanke muku hukun ci dai-dai da abin da kuka ai kata." rokon Abbu suka shiga yi da magiya Abbu ya É—aga waya ya kira yace a zo a tafi da su, aka washe su akayi gaba da su. har aka gama magana Ya SALEEM baice komai ba yana dai zaune yana kallon kowa da ido, har taron ya watse shima ya mike ya fita. su Aunty Rafee'at kam sai murna wai yau asiri ya karasa tonuwa... Da daddaren ranar da aka sallame shi, ina zaune a bedroom É—in Ummi, Ummi ta shigo rike da tray mai É—auke da kayan motsa baki ciki tace "Ke HAMDAH taso ki kaiwa yayan ku." nace "Ni kuma Ummi a bawa Fauzan ya kai masa Allah bacci nake ji." "Maza tashi ki kai masa Fauzan É—in ne zai kai masa ke aikin me kike, in kin dawo kyayi baccin." mike wa nayi ina faÉ—in "Allah Ummi bakiji yan da na gaji ba bai ma fa ce zaici komai ba." "Sai ya faÉ—a ne mutu min da bashi da lafiya." karÉ“ar tray É—in nayi nanufi ko ina bubbuga kafa, kai Ummi ta girgiza tana faÉ—in "Allah ya shirya ko yaushe zaki girma oho." A bakin kofar É—akin sa na cikin gidan na tsaya, nayi sallama ya am sa É—an tsayuwa nayi kaÉ—an dan ban mance dokar sa na idan kayi sallama ka É—an tsaya kafin ka shigo ba, guntun tsaki naja. to ma wai sai nice zan kawo masa abinci. wani tsakin na kuma ja ina shige wa cikin É—akin, da sallama. ya kuma amsa wa, ya É—ago tare da zuba min ido. yana zaune bakin gado sanye da jallabiya, gashin kan sa ya na É—iga da ruwa da alama fitowar sa daga wanka kenan. su Nasmah suna kwance a kan gadon sa suna bacci, nayi mamakin ganin su cikin É—akin na É—auka suna gun Ya Mas'ud ne. a sannu na karaso cikin É—akin na dire tray É—in saman table É—in gefen sa, har lokacin idanunsa a kaina, mike wa nayi ina kokarin barin gurin. naji ya ruko hannuna, a hankali na juyo na kalle sa muka haÉ—a ido, cire idanuna nayi daga nasa a hankali nace "Ya jiki?." bai yi magana ba har zuwa É—an wasu sekonni bai kuma sake hannuna ba, zuwa can ya motsa laɓɓan sa yace "Naji sauki." hannuna na zame cikin nasa naÉ—an matso bakin gadon ina kokarin É—aukar su Nasmah najiyo maganar sa, "Ki bar su a nan." a hankali na juya nafita a É—akin dan kallon da yake min yafara min yawa... Washegari da safe bayan nayi wanka na shirya cikin doguwar rigar les nafito parlour, Ummi tana ta kiciniyar haÉ—a breakfast, tana gani na tace "Yauwa HAMDAH zo ki kaiwa yayan ku breakfast É—in sa." baki na turo na rasa me yasa Ummi take son lallai sai ni zan rika kai masa abinci. tace "Kiyi sauri mana kin san zai sha magani yakamata ya fara cin abinci kafin ya sha." É—aki na koma naÉ—au gyale nafito na karÉ“e tray'n data shirya masa kayan breakfast É—in ciki na yi waje. da sallama na shige É—akin suna kwance kan gado shi da su Naseem sai zuba masa surutu suke, shiko sai murmushi yake binsu da shi. na dire tray'n naÉ—a go ina faÉ—in "Ina kwana, ya jiki?." lumshe idanunsa yayi tare da buÉ—e su a kai na ya kura min ido sosai, ganin haka da sauri na juya zan fita naji maganar sa "Wa zai bamu breakfast É—in idan kika tafi?." baki na murguÉ—a a kasan raina nake faÉ—in "Jimin samin guri ko da ni nake bashi da zai wani ce wai idan na tafi wazai bashi, badun banson ran Ummi na ya É“aci ba an faÉ—a masa zan zo É—akin ne ma." É—an gajeren tsaki naja karaf muka haÉ—a ido da shi, farr nayi da ido na dan nasan yaji kuma nasan baya son tsaki. ganin yana bina da kallon tuhuma na tsakin dana masa, sai na kaÉ—a kwayar ido na tare da murguÉ—a baki. na dawo cikin É—akin naÉ—an sun kuya nasoma haÉ—a musu abin karin, da sauri na É—ago jin hannun mutum a kafaÉ—a ta na juyo cikin hanzari, sai ganin sa nayi daf da ni, ganin yan da mukayi daf da juna a hankali nayi baya da kafata ina kokarin matsawa baya. sai ya ruko kafaÉ—u na gaba É—aya, ya jefa idanunsa cikin nawa yana yi min wani irin kallo, da sauri rumtse idanuna dan sam bana iya jure wa kallon nan nasa, a sannu yashiga motsa laɓɓan sa yayin da nake jin idanunsa suna yawo cikin jikina "Yau she kika zamo haka?." cikin tsiwa na ware idananuna a kan sa nace "Tun shekaru biyar zuwa shi da da suka wuce." shiru yayi tare da sauke idanunsa kasa da alamun jikin sa yaÉ—an yi sanyi da abun da na faÉ—a, na faÉ—i hakan ne kuma domin na tuna masa da baya da kuma abun da ya faru a baya, tun kuma bayan faruwar haka na daina jin tsoron sa. a hankali ya sake kafaÉ—a ta ni ko na juya na fita... Bayan kwana uku kullum ni Ummi take sawa na kai masa abinci ina kai wa kuwa zan juya, ko gaisuwa bana tsayawa yi masa zan fita, kullum su Naseem suna gurin sa a can suke kwana. yanzu shirye-shiryen koma wa Abuja nake dan sai kira nake samu daga ma'aikata na. Da daddare har na kwanta Ummi ta shigo tace na tashi na kai masa abinci, na mike na É—au hijabi na saka kan kayan baccin da ke jiki na na nufi É—akin sa. yana zaune bakin gado su Nasmah suna kwance a gefen sa suna bacci, na juya zan fita ya dakatar da ni ta hanyar rike min hannu, na juyo gare shi zan yi magana, yakai waya kunnen sa tare da faÉ—in "Mamie su Nusaiba su zo." jim kaÉ—an Nusaiba da Fauzan suka shigo, yana rike da ni bai sake ni ba kuma baiyi magana ba, yace da su su É—auki su Nasmah su kai su gun Mamie. suka kwashe su suka fita da su. ya É—an dube ni yace "Ahmad fa?." "Yayi bacci." nafaÉ—a ina mai mamakin yadda akayi yasan sunan sa. a hankali ya saki hannuna ya mike ya taka zuwa bakin kofa ya rufe da key. da sauri nace "Ban fita bafa ka buÉ—e zan fita." juyo wa yayi ya zo bakin gado ya zauna kana ya miko hannu ya ruko hannuna sannan yafizgo ni na faÉ—o jikin sa, hannayen sa duka biyu ya saka ya zagaye ni da su, kokarin fisge jiki na nake da kyau ya daÉ—a gyara rukon da yamin, kana ya mike dani a jikin sa ya haye gado can kuryar gado ya dire ni. da sauri na mike zaune nace "Ka bani key na buÉ—e na fita." kwanciya yayi a gefe na a hankali yake faÉ—in "Nasan Ummi zata kula da Ahmad ki kwanta a nan bacci zaki taya ni." cike da tsiwa nace "A sabo da me zan kwan ta anan ni ka bani key na tafi." ya tsarsa ya É—aura kan baki tare da faÉ—in "Shiiiit ban son hayaniya kwanta nace." yayi maganar yana tsare gira alamun ba wasa suffarsa na Ya SALEEM É—in da na sani a da ya bayyana, sai naji suffar tasa da kwarjinin sa ya cike ni, kasa nayi da kai na batare da na kwanta ba ban kuma iya cewa komai ba. a hankali ya mika hannu ya sauke kan nawa yaÉ—an matse a hankali cikin yin kasa da murya irin na mai jin bacci yace "Kwanta mana HAMDAHHHH ko ke bakya jin baccin ne." har cikin Æ™waÆ™walwa ta najiyo sautin muryar sa da yan da yakira suna na, karo na farko a haÉ—uwar mu da shi na biyu ya kira ni da suna na a kuma irin yanayin da yake kira na a da, a duk san da ya kira ni da suna na sai naji kamar shi kalar yadda yake faÉ—in sunan da ban ne dana kowa. ya janyo ni tare da gyara min pillow na kwanta gefen sa, a hankali yakuma furta "A kwai maganin da zan sha cikin dare ina so ki tashe ni ne dan na sha." mamaki ne ya kama ni wani magani ne kuma ake shan sa cikin dare ban taÉ“a jiba. a hankali ya lumshe idanunsa, ido na É—an kurawa fuskarsa yaÉ—an rame ya kara haske hancin nan nasa ya daÉ—a fitowa zarr sajen sa zuwa zagayayyen É—an gemunsa a kwance suke luf-luf sai sheki suke, san da idanuna ya sauka kan lips É—in sa da sauri na lumshe idanuna bana so na shagalta da kallon sa. É—an numfashi ya sauke kana a hankali ya É—ago hannunsa batare daya buÉ—e idanunsa ba ya zare hijabin jiki na sannan ya saka hannunsa ya zagaye ni, nan ma wani numfashin yakuma sauke wa, jin a iya nan ya tsaya bai kuma yin motsi ba, nakai tsawon awa guda idanuna biyu ganin dai baccin yatafi da shi sai nima na lumshe idanuna babu jimawa bacci yayi gaba da ni... Washegari nayi nayi ya buÉ—e min kofa da asuba na tafi yaki, dana matsa yace kada na cike shi da surutu, a É—akin duk muka yi salla. koda gari yayi haske Knocking É—in kofar da ake ne yasa shi mike wa yaje ya buÉ—e kofar, Naseem ne da Nasmah sai Mamie da Abbu Abba Ummi da kuma Bappa. ina ganin su da sauri na gyara zama ta, tare da sun kuyar da kaina kasa cikin jin kunya, Allah ma yaso da hijabi a jikina. suka karaso cikin É—akin suna yi masa ya jiki, yace "Da sauki." cike da jin kunya nashiga gai da su Bappa, suka amsa suna tambaya ta ya mai jiki. nidai bance komai ba dan kunya yaga isa ta, Ahmad dake rike a hannun Ummi yashiga mika wa Ya SALEEM hannu yana tsalle a hannun ta alamun zaije gurin sa, cikin gwalaÉ“en sa yake faÉ—in Daddy Daddy. wasu zafafan kwalla ne suka ciko ido na, cike da tausayin É—an dan nasan gani yake kamar mahaifinsa ne Ahmad. murmushi Ya SALEEM yayi ya mika hannu ya karÉ“e sa yana cigana da yi masa murmushi har sai da fararen jerarrun hakoran sa suka bayyana, ina ganin su Abbu sun fita nima da sauri na mike nabi bayan su, su Nasmah kuma suka zauna a gurin sa. har dare su na gurin sa har da Ahmad. a daren ranar ma dana kai masa abinci, hana ni tafiya yayi yasa aka kwashi su Naseem da sukayi bacci a ka kaisu gun Mamie dukan su, washegari ma har sai da su Abbu suka shigo duba shi kafin na fita, ina mai jin kunyar su... Yau kam na É—aura aniyar bazani É—akin sa ba, da wuri nayi shirin kwanciya ta na haye gado, Ummi ce ta shigo tarike baki tana faÉ—in "Ikon Allah wai ke sai an ce ki kai masa abinci kafin ki kai masa, kwanciyar ki kikayi wazai je ya kula da shi, amma dai kin san ba lafiya yake da shi ba ko." da sauri nace "Ummi shi yaro ne da sai an kula da shi dan bashi da lafiya, nima kai na ciwo yake min a bawa Fauzan ya kai masa." tace "Ungo naki tashi maza in kin je can É—akin nasa kya sami magani ki sha, yo dan tsiya wazai kullar miki da shi kina matar sa abincin da nake masa ma taimakon ki nake ai kin san dai aikin ki ne, shashancin banza maza tashi ki kai masa." baki na turo gaba na mike kamar na saka ihu ina buga kafa nayi waje, nacika har wuya haushin sa ya kamani "Sai kace wani karamin yaro." nayi maganar a fili ina jan tsaki. ina shiga É—akin na dangwara masa abincin najuya da sauri, har na É—aura hannuna jikin handle ina kokatin buÉ—e kofar na fita, najiyo muryar sa haÉ—e da É—an tari tari yace "Zo ki bani magani na a can na sha." naÉ—an juyo ina kallon in da yake nuna min saman bedside, kamar na tafi abina ganin yan da ya damie kirjin sa yana É—an jan numfashi da taunar lips É—in sa, sai na juyo a hankali naje na É—au magani haÉ—e da gorar ruwa da cup dana gani a gun, na zo gaban sa na mika masa maganin kana na siyaye ruwan cikin cup na mika masa, ina tsaye ya sha ya miko min cup haÉ—e da maganin. ido na shiga rabawa cikin É—akin ganin ban ga su Nasmah ba nasan har ya sa an kaisu gurin Mamie. ina aje maganin na juya zan fita nakuma jiyo muryar sa yana faÉ—in "Zo ki rufe ni." koda na juyo naga yakwan ta yaÉ—an dunkule guri guda da alama sanyi yake ji, baki na taÉ“e a raina nace "Ba dole kaji sanyi ba a sanyin nan singlet da gajeren wando ne ajikin mutum gakuma AC na aiki." na iso bakin gadon na ja blanket na rufe masa jiki, zan juya sai jin hannun sa nayi cikin nawa ya janyo ni na faÉ—a jikin sa,ina kokarin mike wa ya gyara min kwanciya gefen sa tare da rufe ni da bargon ya janyo ni jikin sa sosai har muna gogar juna. "Sanyi nake ji." yayi maganar yana tura hannayen sa duka biyu cikin riga ta yana mai daÉ—a janyo ni jikin sa, tafin hannun sa sun É—au zafi rau sai daÉ—a cusa su yake cikin jiki na yana niman mafakar da zai aje su, gaba ki É—aya jikin sa yayi zafi har ina jin zafin yana rasa ni, shiru nayi ina jiyo sautin bugun zuciyarsa, sai fidda numfashi yake da É—an sauri sauri. a É—an tsorace ganin halin da yake ciki nace "Ya SALEEM ko na kira su Abbu ne jikin ka yayi zafi sosai, ko za'a koma asibiti." cikin É—an jan numfashi yace "A'a su ba zasu iya yimin maganin komai ba ke ce maganin ina jin sanyin sosai kiyi wani abu na daina ji." É—an shiru nayi ina tunanin maganar nasa, kankame ni yayi sosai a jikin sa kana ya cigaba da magana wan da maganar tasa a hankali yake fita haÉ—e kuma da sautin numfashi, "Ki taima min wajen samar min da É—umi a jiki na na tabbata ke kaÉ—ai zaki iya." shiru na kuma ina tunanin ta ina zan fara kamar yadda yace É—in, sake ni yayi a sannu yaÉ—an yunkura ya zame singlet É—in jikin sa, kana ya É—ago ni ya zare rigar baccin dake jiki na, yarage sai bra da kuma wandon rigar. da fari nayi kokarin dakatar da shi daga cire min rigar da yake yunkurin yi, sai dai ganin yadda yake rawar sanyi da faÉ—in sanyi yake ji, sai na hakura da kuma ganin bayyi yunkurin cire min bra ba. rungume ni yayi kamar zai cusani cikin kijin sa yarika mannani da jikin sa, yayin da ya saka fuskarsa gefen wuya na yana juya fuskarsa da manna shi a fatar wuya na. yarika yin haka har muka kwanta kan katifa, ya kan kame ni gam-gam ko kyakkyawar motsi ba na iya yi, magana ya soma cikin jan numfashi "HAMDAHHHH kar kiyi nesa da ni dan Allah kada ki kara yin nesa da ni, na tabbata kika sake bari na babu ko shakka yanzu kam mutuwa zanyi, ban san yanda zan misalta miki yadda nake ji cikin zuciya ta ba, amma ki sani zan iya mutuwa idan kika kuma bari na, kiyi min alkawarin bazaki sake bari na ba, zaki zauna dani duk wuya duk rintsi ina mai baki hakurin abun da ya faru, amma ki sani bada sona hakan ta faru ba." ture sa na shiga yi ina faÉ—in "Idan bada son ka ba tilasta ka akayi, ka wulakanta ni ka tozartani kayi min kazamin kazafi da tabo mai muni, ka kazantamin Æ´aÆ´a na kasa mahaifina yayi min korar kare kasa Ummi na ta zubda hawayen ta, kasa na shiga duniya rayuwa ta takusa salwanta har da na Æ´aÆ´a na da basujiba basu gani ba, Ya SALEEM bazan taÉ“a yafe maka ba, ka sani ka rabu da ni babu wani yafiya saka nin mu, wannan komawar auren kaddarar zan karÉ“e sa zuwa san da zaka gama samin lafiya zan yi tafiya ta nayi nesa da nan bazaka sake gani na ba, kaje ka zauna da matar ka mai gaskiya wacce bata karya bata kuma kawo maka wani gardi gida da cikin shege gida ba da auren ta, ni kuma zan zauna da nawa halin a haka da kuma Æ´aÆ´an da basa da uba sai uwa a duniya." da karfi na ke ture sa ina son kwatar kaina, ganin ko kyakkyawar motsi bana yi cikin hannunsa. sai kawai na saki kuka ina cigaba da ture sa da faÉ—in "Ka sake ni ka rabu da ni." lips É—in sa ya taune da karfi tare da rumtse idanunsa yayin da sautin bugun zuciyarsa ya karu. fuskar mu ya haÉ—e guri guda, yana goga fuskar sa kan nawa, yaÉ—an fisgo numfashi kana yace "Kiyi hakuri dan Allah ki mance da kukkanin abun da ya faru cikin duhu babu haske, ki kuma daina dan ganta min Æ´aÆ´a na da mara sa uba." nayi matukar mamakin jin fitar kalmar hakuri daga bakin Ya SALEEM wai ni yau yake baiwa hakuri, cikin tattausan lafazi da sigar lallaÉ“i da kuma neman gafara haÉ—e da sulhu. ganin numfashin sa yana yin sama-sama da sauri na haÉ—iye kukan ina faÉ—in "Ya SALEEM na kira su Abbu ko Dr Farooq?." kai ya girgiza min yana ta kokarin janyo numfashin sa, tsoro ne ya kamani sosai ganin yan da yake yi sai na shiga jera masa sannu a kiÉ—ime. kansa ya É—an É—ago da kyar yana kallon cikin kwayar idona yakuma yanyo numfashi da kyar kana yace "Ke ce maganin idan kika yafe min nasan zan warke." da sauri nace "Nayafe maka nayafe maka Ya SALEEM." wani murmushi ya sake har sai da hakoran sa suka bayyana, a hankali ya sauke lips É—in sa kan nawa ya tsotsi baki na sosai kana ya zare bakin sa tare da faÉ—in "Nagode." kwanciyar sa yaÉ—an gyara batare daya sake ni ba, har kuma lokacin numfashin sa bai dai-dai ta ba, lamo nayi a jikin sa ina jiyo bugun zuciyarsa, a sannu a hankali bugun zuciyar tasa da kuma numfashin sa suka fara dai-dai ta, har sukayi normal. idanunsa a lumshe kamar mai yin bacci fuskarnan tasa yayi fayau da shi. numfashi naÉ—an sauke ganin ya sami salama daga halin da yake ciki hatta zafin jikin ma babu shi yanzu, a hankali nashiga kokarin zame jiki na, sai ji nayi ya daÉ—a rike ni gam da sauri na kalli fuskarsa idanunsa a lumshe, sai na mai da kaina a raina ina ayyana idan baccin sa yayi nisa zan tafi abina, ban san san da bacci ya É—auke ni ba sai kiran sallar asuba najisa a kunne na. ko da na buÉ—e idanuna baya gadon, jin karar buÉ—e kofa yasani kallon kofar bathroom, jikin sa na É—iga da ruwa da alama wanka yayi, a sannu ya tako bakin gadon ya dube ni da kyau kana yace "Taso kije kiyi al'wala kizo muyi sallah." yayi maganar yana ruko hannuna tare da mikar da ni zaune, ganin yan da yake bina da wani irin kallo da sauri na kalli in da yake binsa da kallon, cikin hanzari na janyo blanket narufe kirji na, na gama mance wa babu riga jiki na sai bra, baki na É—an turo tare da janyo riga ta na saka kana na mike na shige bayin, sai da na wanke baki na da burosh É—in sa kana nayi wanka sannan na É—auro al'wala na mai da kayan da na cire na fito. a kan sallaya na same sa yana zaune yana azkar, yana gani na ya mike tare da É—aukar hijab É—ina dake bakin gado ya mika min na saka, kana na tsaya bayan sa yaja mana sallar ko da muka idar addu'a sosai ya rika kwararo mana na neman kariya da samin falalar Ubangiji. muna shafawa na mike "Zo mana." ya faÉ—a yana mike wa kan sallayar bakin gado ya zauna, a hankali na tako in da yake, sai ya ruko ni yace "Zo ki rufe ni na fara jin tsanyin." sakiyar gadon ya haura nima na hau ina kokarin jan bargo na rufe shi, sai ya janyo ni na faÉ—o jikin sa. ya zagaye ni da hannayen sa, a sannu ya mirgina ni zuwa kasa shi ya dawo sama na, hijab É—in jikina ya zare kana a hankali kamar maiyin raÉ—a yace "Zaki taya ni hira?." kai na girgiza da sauri nace "A'a." idanunsa ya lumshe tare da kuma buÉ—e su cikin nawa sannan yace "Please ki gwada dai." kai na girgiza a lamar a'a dan yafara sanya min kasala da narkakkun idanunsa, sai naji baki na yayi min nauyi. asannu yashiga kissing É—ina da shafa ni, yakuma tare ni ta in da bazan iya motsawa ko yunkurin dakatar da shi ba, cikin kankanin lokaci ya kashe min jiki da salon sa, har ya sami nasarar zare rigar jiki na, a sannu ya kife fuskarsa sakankanin ababen kirji na ya zura harshen sa yana latsar tsakiyar su da gefe da gefen su, gantsare wa nayi jin yan da harshen sa ke yawo sakankanin nonuwa na, hakan dana yi kuwa ya bashi dama wajen zura hannunsa ta kasan baya na, ya É“alle maÉ“allan bra na a sannu cikin wani irin salo mai wuyar fassara ya zare bra'n. wani nannauyar numfashi ya sauke, yakafe ababen kirji na da ido, wan da suke tsaye kyam sun cika tip-tip tamkar babu É—an da ya taÉ“a sha, kana ya É—ago hannunsa da tuni suka kama É“ari ya sauke su kan ababen kirji na, wani irin cafka yayi musu tare da kuma sauke numfashi, nan yashiga shafa su da matse su kana ya kafa bakin sa kan É—aya yayi masa kyakkyawar cafka tamkar zai cinye shi. yarika tsotsar sa yana kuma matse É—ayan, sai da ya tsotse su son ransa kana yaÉ—a go yayin da gaba É—aya jikin sa ya É—auki É“ari ya zare wandon jiki na, ina kwance ko yatsa ta bana jin zan iya É—agata dan gaba É—aya ya gama kashe min jiki da salon sa. jallabiyar jikin sa ya zare haÉ—e da boxes, nan ya cigaba da latse jiki na tundaga kan nonuwa na har zuwa kan HQ É—ina jin yanda yake juya tongue É—in sa cikin HQ É—ina yasani bankare wa tare da cusa hannuna cikin sumar kansa. "Ya SALEEMMM ka bariiiiii." nayi maganar jiki na na É“ari, sama yayi da hannunsa batare daya ciro bakin sa ba ya zura min yatsar sa cikin baki ba shiri na cafke yatsar nashiga tsotsar sa. sai da yagama birkita ni ya kuma birkita kansa kafin ya É—ago yayi min rumfa yana karanto addu'a. da sauri ya shige ni a tare muka sauke numfashi a fili, kamar dai da suna na yarika kira yayin da yake sama da kasa a kaina kamar jarumin dokin daya sami katon fili yake sukuwar sa son ransa, Ya SALEEM jarumi ne bana wasa ba ina daÉ—a tabbatar da hakan ne a duk san da ya kusan ce ni, a yauma na daÉ—a gaskata hakan dan kuwa na gurzu a hannunsa bana wasa ba, sai da na nimi daya yi hakuri ya kyale ni. bayan yasami sauke abin da ke cikin matar sa yayi lamo a kaina yana maida numfashi, a hankali ya zare jikin sa ya kwanta gefe tare da janyo ni ya rungume ni a jikin sa sosai, yayin da yake jin sa wasai tamkar an zare masa ciwon da ke damin sa. idanuna na lumshe ina mai sauke numfashin gajiya, a hankali ya shafi gefen fuskata a sannu na buÉ—e idanuna muka haÉ—a ido da shi, lallausar murmushi ya sakar min kana ya mike ya shiga bayi, yana mai jin zuciyarsa wasai, siffofin HAMDAH ne kaÉ—ai ke yi masa yawo a ido yan da yaganta ta kara cika ko ina ya ciko tip-tip da shi sai tsole idon mai kallon sa yake. yana wankan yana sakin murmushi lokaci zuwa lokaci, yadda ya sami HAMDAH bayyi zaton samin ta a haka ba sai kuma tayi masa ba zata dan yadda ya jita sai yake jin taÉ—are sanin sa a da' bayan yayi wanka ya fito, ya karaso baki gadon yaruko hannuna yana faÉ—in "Taso kiyi wanka." ina mike wa da sauri na koma na zauna ina mai mamakin kaina dajin abin da nake ji a duk san ya ya kusan ceni a wancan lokacin, hakika Ya SALEEM na daban ne. "Yaya dai." yafaÉ—a yana mai ruko ni da sauri, hannu na yarfe nace "Jiri nake ji." kansa ya É—an dafe tare da faÉ—in "Oh sorry na mance zauna bari na samar miki abin da zaki ci." tea ya haÉ—o mai kauri ya mika min na sha kana ya taimaka min na mike naje nayi wanka, yana tsaye har na gama duk motsin da zanyi idanunsa a kan bottom da breast É—ina. ina fita na saka kaya da sauri na fita a É—akin, gudun kada su Mamie suzo naji kunya...... Kwana na goma yau na É—aura aniyar komawa saboda kiran danake ta samo daga can, banbi ta kan Ya SALEEM ba na sami Bappa na sanar masa dan nasan inta shine kam bazai barni na koma ba. Bappa yasame shi da maganar yace bazan tafi ba ko zan tafi ba yanzu ba, sai da Bappa ya nutsar da shi da kyau game da ayyuka na, da kyar ya amince na tafi... kwana na uku da dawowa ya biyo ni, ranar da yazo yace shi bazai bakwana a side É—ina ba,Bappa yayi dariya yace yasan abinda yake damin SALEEM kishi ne kawai kishin ma da wan da ya mutu, a side É—in ba'ki ya kwana, washegari kuwa can naje na taya sa kwana. washegarin kwanan sa na uku tun da yafita da safe sai yamma ya dawo yana dawowa yace, mu tattara mu koma gidan sa dan shi bazai zauna cikin gidannan ba, Bappa yace gidan nasa a ina yake kuma yaushe ya siya, yace tuntuni yana da abinsa yau kuma yasa aka zuba komai na amfani. a daren ranar aka raka mu sabon gidan sa, babban gida ne sosai dan girman sa ya kai wan da muka baro, an shirya komai na more rayuwa. wancan gidan kuma nace su Abbu su dawo ciki su zauna da su Bappa cikin wata É—aya nasa aka rushe É—aya side É—in gidan da Mama da su Talatu suke zaune ciki aka gine shi iri É—aya da ginin side É—ina, Abba da Ummi suka dawo É—aya Abbu da Mamie suka zauna a É—ayan. kana aka gine wani gefe guda É—an dai-dai Mama ta koma ciki, gidan mu na Bauchi kuma a ka kulle shi, aka barshi na saukar mu idan muka zo Bauchi ko wani hidima idan ta tashi acan muna da masaukin sauka ciki, gidan Ya SALEEM kuma ya barwa Ya Mas'ud dan shi bai dawo Abuja sabo da aikin sa, yace idan yayi aure yasaka matarsa a ciki...... Bayan wata uku da komawar mu sabon gida Aunty Rafee'at ta haihu, muka tafi bauci duka har da su Ummi. bayan suna da kwana biyu, mukayi shirin koma wa, motar su Ummi ya riga namu tashi dan Ya SALEEM ya fita bai dawo da wuri ba, ya na dawo yakwashe mu, muna fita daga layin unguwar mu kira ya shigo wayar sa bayan ya sun gama magana da wan da ya kira shi ya dube ni cikin kula yace "Wani aboki na ne nayi masa alkawarin haÉ—uwa da shi idan nazo yanzu yake tuna min da hakan, bari mubi gurin sa sai mu wuce daga can." nace to, yajuya akalar tafiyar izuwa gurin abokin nasa, a bakin get É—in wani asibiti yayi hon a ka buÉ—e get É—in yasa kai ciki, yana dai-dai ta parking muka fito, yana É—auke da Ahmad yayin da yake rike da hannun Naseem, niko ina rike da Nasmah muka nufi cikin asibitin, a bakin kofar da zai sada mu da cikin asibitin muka haÉ—u da abokin nasa, gaisawa irin na abokai suka fara tare da É—an zolayar juna, abokin nasa ya dube ni yana faÉ—in "Madam da so kike ki tafi da shi baki bari mun haÉ—u ba ko." dariya nayi tare da gaishe sa ya amsa yana yiwa su Naseem wasa, ya dube Ya SALEEM yace "MuÉ—an je daga can kada wari ya dame ku anan." Ya SALEEM yace "Wari kuma ina ma'aikatan naka suke da bazaka sa su gyara maka cikin asibitin ba, ai hakan sai ya iya karawa masu jinya ciwo." yace "Wlh kai dai bari wata mara lafiya ce ke wannan warin ba datti ba,yanzu haka da nake faÉ—a maka ta kora min kostoma, duk wani wan da zai kawo majinyaci nan da zaran ya shigo yaji wannan warin sai ya juya da majinyacin sa,waÉ—an da suke nan kafin ta fara wannan warin suma suka tattara sukayi gaba, hatta Æ´an'uwan ta kasa zama sukayi a kanta sai kuÉ—i suke turawa na jinyar ta, to suma inaga yanzu sun gaji ne dan wata biyu kenan rabon da suturo da kuÉ—in, nima yanzu nagaji sallamar ta zanyi nasa a tattara ta akai ta duk in da tace a kaita dan zata kashe min kasuwa." kai na jinjina cike da tausayin matar, nace "To me ya same ta haka wani irin cewo ne gare ta?." yace "Wlh hatsari tayi tasami kariya a kafa da hannu an É—aure kafan bayyiba karshe ruÉ“a yayi dole sai an yanke kafar shine yake wannan warin, Æ´an'uwan ta kuma su kawo kuÉ—in ai kin sun gagara gashi nan ta ishe mu da wari." Ya SALEEM yace "KuÉ—in har nawa ne haka?." yace "Miliyoyin uku." kai na girgiza ceke da jin tausayin ta nace "Ayya ko zamu iya ganin ta?." ido ya waro yace "Wa wai kushiga inda take?, ai bazaku iya ba tana cikin É—aki kofa a kulle wari yana fito wa har nan ta ya zaku iya shiga inda take." nace "Zan iya muje na gaishe ta, Allah ban ganta ba amma tausayin ta ya cika ni." "To muje in zaku iya." yafaÉ—a yana shige wa gaba muka bi bayan sa. sai da ya shiga office É—in sa ya É—auko turare haÉ—e da facemax ya bamu muka saka kana yayi gaba yana fesa turare muna biyo shi har muka isa bakin kofar É—akin da take ciki. sai da ya shiga ya fesa turare mai yawa kafin yace mu shigo, muka kusa kan mu ciki, duk da turaren da ya fesa bai hana É—akin tashi da wari ba, kamshin turaren daban warin shima da ban. ido na kurawa matar dake zaune a kan gado kuda suna binta, ina ta son tuno in da na santa. hannun ta na É“ari ta shiga nuna mu tana faÉ—in "HAMDAH SALEEM." sai kuma ta fashe da kuka, da mamaki nake kallon ta nace "Na'ima ke ce?." kuka sosai take tana faÉ—in "Dan Allah dan Allah HAMDAH ki yafe min kinga yanda Allah yayi dani ko kowa guduna yake, nakuma san alhakin ki ne ke bina, ki yafe min na roke ki, SALEEM dan Allah ku yafe min, HAMDAH ina É—an da kika haifa na roki gafarar sa ko shima zai yafe min. Naseem da Nasmah na nuna mata nace "Gasu nan." hannu ta miko tana faÉ—in "Kuzo ku yafe min ko zan sami sassauci gurin mutuwa." da sauri Ya SALEEM ya janyo su jikin sa tare da binta da mugun kallo yace "Kul kada ki sake ki taÉ“a min yara." ya sasu gaba sukayi waje ina kiran sa bai ko saurare ni ba. kuka Na'ima ta kuma fashewa da shi tana cigaba da niman gafara ta, kwalla na share nace "Na yafe miki Allah ya yafe mana duka, Allah kuma ya baki lafiya." godiya ta shiga min ba kakkautawa, na fita ina yi mata Allah ya sawaka, a cikin mota na tadda su Ya SALEEM sai tofar da yawu yake rantsa a É“ace. a take a gun na karÉ“i account É—in Dr nayi masa transfer É—in kuÉ—in da ake nema ayi mata aikin, nace "Ayi mata aikin dan Allah cikin gaggawa dan naga alama tana jin jiki sosai." yace "Insha Allah za'a yi sa cikin gaggawa tun da ga kuÉ—i ya samu." ina shiga motar Ya SALEEM ya figi motar da gudu bai ko tsaya yi wa abokin nasa sallama ba. har mukayi nisa babu wan da yayi wa wani magana,har lokacin kuma fuskarsa babu annuri, kamar an zabure sa cikin faÉ—a ya kalli inda nake yace "Matar da taso hallaka rayuwar ki dana Æ´aÆ´an ki wai ita kike jin tausayi, ko yau ta tashi sai ta nimi abin da zata hallaka ki da shi, ita ba abin tausayi bace, wai har kuÉ—i kika biya ayi mata jinya, to bari kiji har idan kinsan kuÉ—in maraya kika É—auka kika bada ayi mata aiki dashi, kiyi gaggawar maida masa abin sa dan nasa ne ba naki ba." murmushi nayi nace "Ayya Ya SALEEM wlh ta ban tausayi ne, idan muka yafe mata Allah shi ma zai gafarta mana, kuma ba kuÉ—in Ahmad na bada ba kuÉ—i na ne, kai ma kayafe mata dan Allah." a fusa ce yace "Bazan taÉ“a yafe mata ba kin san girman laifin da ta aikata min kuwa! ta raba ni da ke da kuma Æ´aÆ´a na, shi ne kike cewa na yafe mata!!." ya karasa magaran cikin karaji. kai na girgiza nace "To ba gashi mun dawo gare ka ba yanzu, babu abun da baya wucewa." ganin bai kuma magana ba sai huce yake, nasan ransa ya É“aci sosai, a hankali na É—an matso tare da kwantar da kaina jikin kafaÉ—ar sa. nasaka hannuna nazagaye shi, numfashi ya sauke a fili kana yayi kasa da idon sa ya kalle ni, murmushi na sakar masa, yawani lumshe idanunsa tare da kuma sauke numfashi. da sauri na tashi a jikin sa nace "Ya SALEEM ka buÉ—e idon ka karkasa mu faÉ—i." ya buÉ—e idon a kaina tare da sakar min murmushi mai sanyi..... Bayan shekara É—aya zaune nake a parlour natasa katon ciki na gaba Ya SALEEM ne suka shigo shi da Naseem da Nasmah da Ahmad. tun kan ya karaso yake bina da murmushi yaran ko da gudu suka iso in da nake zasu zube kaina, da sauri Ya SALEEM ya É—aga kafa ya taro su yana faÉ—in "Kai ku tsaya kada ku danne baby ciki mana, ku zauna a nan." ya zaunar da su gefe kana ya zauna gefe na tare da shafo ciki na ya ce "Wai yaushe zaki haifo mana babyn mun masu mu gansa fa." baki na turo nace "Nima na matsu na sauke na huta." Naseem yace "Mommy yaushe zaki zamo mana baby." baki na turo banyi magana ba Ya SALEEM yaÉ—an yi karamar dariya yace "Bashi amsa mana,yauwa Naseem me kake so a haifo mana mace ko na miji?." baki ya washe yace "Namiji." yace "To Aunty Nasmah fa me kike so a haifo mana?." tace "Daddy na mace." ya ce "To duk naji naku saura na my Ahmad É—ina, kai me kake so?." yace "Mace na miji." dariya mukayi dukan mu nace "To kai duka kake so mace da na miji kenan." rungume shi Ya SALEEM yayi yana faÉ—in "I love You my son Allah ya kawo su masu albarka irin ku." dariya nayi ina kwantar da kaina jikin kafaÉ—ar sa, gefen fuska ta ya shafo yace "Inayi miki son da baki ba zai iya furta wa ba, idanuna na lumshe ina sakin murmushi, nikam nasan nayi dace a rayuwa ta da kallamar sona Ahmad ya mutu gashi a yau gorzo jarumin maza ABDALLAH IDRIS ABDALLAH yana faÉ—a min girman son da yake min a zuciyar sa wan da baki bazai iya furta wa ba sabo da girman sa. hakika ni HAMDAH nagodewa ALLAH...............! TAMMATBIHAMDILLAH Ina godiya wa tabaraka ma É—aukaki mabuwayi mai izza da ya nuna min wannan rana da littafin nan ya kawo karshe, ina yiwa É—aukacin masoya fatan alheri....