*TMWBK301* *TMW is a paid Novel, Pay 500 for regular or VIP N1K, Via 0552179550 Jamila Umar Gt bank, 09069067488* https://chat.whatsapp.com/IhAz8h8nRy250ZnGGXwM65 *LAME NIG!* *KASAITATTUN MATA MUN GAISHE KU*. *AISHA LAME TA KAWO MUKU DUKKAN NAU'IN KAYAN KWALLIYA*. *KUNSAN GWANAACE WAJEN BAWA FATA HAKKIN TA* *KUN TUNA KYUAN FATAR GUDUYO KO?* *KUN TUNA DAI YADDA BULKACHUWA KE SIYAWA YABI KAYAN KWALLIYA NA ORIFLAME KO?* *TO KEMA GARZAYO KI ZABI NA KI, KO TA ZABA MIKI WANDA ZAI FI DACEWA DA FATARKI*. *BA IYA KAYAN ORIFLAME BA KAD'AI.* *TANA DA PRODUCTS DABAN DABAN MASU KYAU, MASU MASTAKAITAN FARASHI*. *KU TUNTUBE JIKAR DADAR MARINA A WANNAN LAMBAR 07036662633*. *ADO DA KAMSHI NE SIRRIN GAYU* Ina tafe ina hard'ewa kamar zan Fad'i saboda sauri da waige waige, burina kawai na yi nisa da gidansu Assadiq kafin abunda na ke gudu ya faru dani. Ni dai a sanina babu wanda yaga fita ta sannan har na fara nisa ban ji takun wani na bin bayana ba. Har na cire mayafina a saman fuskana na saki jiki na fara tafiya ina Duba abun hawan da zan samu ya kaini tasha. Kamar daga sama naji an kira sunana da karfi "HASIYA..!" Gabana ya fad'i ras! Jikina ya fara rawa na kasa juyawa Saboda Tsabar Rude'wan da na yi sai naji kamar Muryan Assadiq. Tahir bai jira sai Hasiya ta juyo ba ya taka ya sha gabanta, cikin mamaki na Dago ina kallonsa da sakin baki da mamakin me yasa ya Biyo ni? Kuma daman yaga Lokacin da na fita ne? Sai wata zuciyar ta ce min kila Assadiq ne yaga fitar ki ya kuma aikosa wajen ki. Sai naji na samu yar salama kad'an sai dai Lokaci d'aya in ka kalleni zaka san ina cikin yanayin Tsoro da Firgici. Daga sama har kasa ya ke kallona Cikin kallon kaskanci da wulakanci. Sai na sha jinin jikina na maida kaina kasa ina rawan baki na kasa mgana. Cikin kaushin Murya Tahir yace"Ki gayamin gaskiya shin da gaske ne har yanzu akwai aure tsskanin ki da Sadiq? Gabana ya kara bugawa Dam! Da Sauri na Dago ina kallonsa cikin mamakin kalamansa, kara had'e rai ya yi ya na kara kaurara Muryansa yace"Ki gayamin gaskiya in kina so ki Tsira da mutumcinki, in kuma kika yi min karya sai kin raina kanki wlh." Jikina ya fara rawa na fara kokarin ja da baya, da ya ke yadda muke Tsaye ba wanda zai fahimci wani abu za'a yi Tunanin ya Tsaidani muna magana ne. Na rasa me zan ce masa Tunda Assadiq bai bani wannan Hurumin ba, Sannan bazan so na zama mai Tona masa asirin da Allah ya Rufa masa ba gwara na bari in za'a ji komai a ji a bakinsa, kila ma zamana da Assadiq ya zo karshe in na fad'i abunda ke Tsakaninmu zai zo ya lalata komai tunda a kalaman Abokinsa na Fahimci shima ya yi Tunanin Assadiq ya sake ni Tuntuni. Ina cikin wannan Tunanin naji ya Dakamin Tsawa ya na kara fad'in"Kina batamin Lokaci malama ki fad'amin gaskiya ki yi tafiyarki cikin salama in kuma ba haka ba? Umh!" Ya fad'a ya na wani Cije baki, ganin haka yasa idanuwana suka kawo kwallah cikin rawan baki da na gabban jiki nace"Ba ba. Ba komai a tsakanina da shi." Kallon da naga ya na yi min ne yasa na kwaso rantsuwa ina fad'in"Wallahi gaskiya na.." "Karya ki ke fad'amin ba gaskiya ba ne malama." Kalamansa suka katseni ai sai na yi shuru ina raba idanuwana kamar wacce ta yi karya, duk da daman karyan na yi sai kokarin Danne kukan da ke tasomin na ke yi Kada kukana yasa jama'a su fahimci wani abu su taru faruwar haka kuma daidai ya ke da lalacewar komai a wajena ni Hasiya. Tabbas yasan karya ta ke yi, domin Sadiq bazai taba gayamasa abunda ba gaskiya ba ne, tunda ya furta yasan akwai wani abu a kasa. Cikin Daga murya yace"Sadiq ya fad'amin komai akan cewa har yanzu ke matarsa ce, kinga kenan karon Farko kin yi min karya kuma sai da na gargad'eki a kan haka." Ya fad'a ya na nuna ni da yatsa da Sauri na had'a Hannayena waje d'aya ina fadin"Don Allah ka yi hakuri ka Rufamin asiri ka barni na yi tafiyata." Da Sauri yace"Zaki tafi yanzu ammh sai kin fad'amin wa ya kawo ki gidan nan? Ki ka kara gayamin karya wannan karon bazan Daga miki kafa ba." Da Sauri nace"Eh Saliha ce, Saliha ce kawata ita ta gayyaceni." Cikin mamaki ya ke kallona kafin yace"Saliha? Ta ina? Cikin Rawan baki nace"Saliha yayar Assadiq wacce ke aure a garin Ibadan" Cikin Dage gira yace"I see garin ya ya? A ina kuka san juna? Ina goge hanci na fara bashi Labarin farkon had'uwata da Saliha da kuma Dangin Assadiq a kaduna. Cikin mamaki yace"Ke yar'uwan mijin Salima ne? Sai na gyad'a masa kai da Sauri ina goge kwallar da kawo cikin Idanuwana. Cikin mirmishin Mugunta Tahir yace"Wato in na gane kinsan daman Waye Assadiq ammh duk da haka sai da kika zo domin ganin ma idon ki ko? Sai na kasa mgana shi kuma ya Cigaba da fad'in"Good. na ji dadin haka gwara da kika zo, ki ka ga abunda zaki kara Fahimtar cewa Sadiq ba Tsaran auran ki ba ne, sannan ki kara gane cewa ba rayuwarku d'aya ke da shi ba." Ya dakata ya na maida Numfashi kafin ya Daga hannu ya na nuna min gidansu Assadiq lokaci d'aya ya na Fad'in"Kinga wannan gidan? Da duka mutanen da ke cikin shi? Sai na gyad'a masa kai Kamar wacce ta yi karya , bai damu ba ya cigaba da Fadin"To wannan itace hakikanin gaskiyar Rayuwar Sadiq. wacce kika sani a baya ba ita bace Rayuwarsa wannan rayuwar ta karya ce, ita wannan da kika ganin ma idanuwanki itace Zahirin waye Abubakar Sulaiman Abubakar Shinkafi ina fatan kin gane? Da Sauri na gyad'a kai na cikin mutuwar jiki da na zuciya. Shi kuma ya cigaba da fadin"Kinga Iyayensa da Ahalinsa tare da yan'uwansa Uwa uba matarsa, to ina so ki saka a ranki Assadiq din da kika sano a zariya karya ne, Sadiq da kika gani a Gusai shine zahiri, shawara da zan baki guda d'aya ne ki yi nisa da Rayuwarsa domin baki da kofa ballatana Muhalli ki je ki nemi daaidai da ke, daman kuma Daga taimako ne sai kuma abu ya zame masa karfen kafa, Sadiq ya aureki ne Saboda mahaifiyarki ta fad'i Gabansa ta rokesa ta na kuka, ammh bai taba son ki ba, Sultana ce matarsa tun ba yau ba shaidu ne kad'ai ba su shaida ba sai yau, kuma ya yi min alkwarin sakin ki tun a lokacin da zaman mu ya kare a zariya, sannan ya tabbatar min da ya sake ki, ban kuma san me ya faru yanzu naji wani Labari na Dabam ba, to ko ma menene wannan ba shi ba ne a gabana, abunda ke gabana shine ki yi nesa da Rayuwar Sadiq aduk in da ki ke zai aiko miki da Takardan sakin ki" Ya karishe fad'a ya na kallona, nima Tunda ya fara mgana shi na ke kallo cikin mamakin kalamansa. Da gaske ya ke yi Assadiq baya so na? Kuma yace daman in ya aureni zai sakeni? Kamar Tahir yasan abunda na ke Tunani ya fara gayamin yadda suka yi da Assadiq a daran da aka Daura mana aure har zuwa ranar da zasu koma Garinsu bayan sun gama Bautar kasa da ce masa da ya yi ya riga ya Rabu dani bayan ya bani jari mai Tsoka. Bansan ina hawaye ba, sai da naji saukarsu a saman kumatuna, sai dai daga saman lebena ina mirmishi a raina ina fad'in"Tabbas ya bani jari kyakyawan jari a rayuwata." Batare da wani Tunani ba na kalli Tahir ina fad'in"Naji shawaran ka, kuma in sha Allahu zan yi amfani da ita nagode." Da haka na share hawayena da gefen mayafina na rab'a ta gefensa na Cigaba da tafiya, sai da na yi nisa da shi kad'an na tsaida adaidaita na gayamasa tasha zai kai ni yace na Shiga, ina kallon abokin Assadiaq har Adaidaitan da na hau ta fita daga Layin gidan su Sadiq bai bar wajen ba, inaga ya na so yaga tabbacin yin nisa da Rayuwar Assadiq gabadaya. Muna tafe cikin Adaidaita ina Tuna yadda nazo garin Gusau a jiya ina mai Nadamar me yasa na Biye ma zuciyata na zo? Har wajen la'asar ina zaune ban samu mafita ba shed'an ne da kuma kishin Assadiq suka Ingizani na kira Saliha nace ta turomim adireshin gani nan zuwa, nan ta ke ko ta turomin ta na mai Farinciki batare da sanin mijina ko yan'uwana ba na shirya tafiya Gusai a gidan mu Maman suhailat kawai na yi ma sallama itama ban ce mata tafiya mai nisa zani ba, sai ita kuma ta yi Tunanin wajen Amma zani har ta na min fad'an na yi yamma, ballatana yadda Rayuwarnan ta lalace na rashin Tsaro. Sai da na je tasha na hau Motar gusai har mun dau hanya sannan na fara nadama naji kamar na Dawo ammh kuma zuciyata na ingizani zuwa ganin abunda na ke so na gani ko kuma nace na kara samun Tabbaci. Abunda ya faru dani, yau shine abunda Amma ke ta min gudunsa ta fad'amin kada na matsa da sanin abunda ba'a so na sani ba, in na matsa to zan zo na san abunda zai zama tashin hankali a gareni. Shiyasa akace abunda Babba ya Hango yaro ko ya hau kan Rimi bazai hango shi ba. Bansan Lokacin da na fashe da kuka ba, ina tuna Kasadar da na yi sai wajen goma saura na Dare muka iso mota ta lalace mana a funtua sai da aka dad'e sannan aka gyara. Saliha na ta kirana nace mata muna Hanya, sanda muka shigo gusai na kirata na gayamata sai tace na tsaya a tashan tunda dare ya yi zata zo ta Daukeni. Sun zo tare da wata itama yayar Assadiq ne tunda suna da yawa naji dai ta na ambatan sunanta da Yaya Saddiqa, sannan kuma inaga ta riga ta fad'a musu ni yar'uwar mijin Salima ne shiyasa suka saukeni Shashen Mama cikin kyakyawan Tarba. Sai a lokacin naga Salima muka gaisa, yadda ta nuna bata sanni ba, ammh dai ta san Dangin Uban mijinta yan zariya ne. Saliha ke tafe fad'in ta na da kawa yar'uwan mijin Salima, a kaduna muka had'u ga shi har na zo mata Biki, daga dare zuwa wayewar gari na kara yardan ma kaina Rayuwar Assadiq a zariya karya ce wannan itace Zahirinsa, naga ahalinsa gabadaya na kuma kara tabbatar ma kaina cewa shi d'in dan gata ne kuma ya ci sunansa Magajin gida. Naga Umma da Abba, na kuma kara yardan ma kaina da zuciyata Assadiq ya yi nisa da Rayuwata kaddara ce ta had'a zaman mu waje D'aya. Kukan da na ke yi yasa har sai da mai adaidaitan da na ke ciki ya juyo ya na kallona, ni kuma ganin haka yasa na yi Saurin shanye kukana, na koma ina faman goge Hawayena. Ina Tunanin soyayyar da naga ana nun ma Sultana matar Assadiq, ina da yakinin yadda Suke sonta in Labarina ya bayyana a garesu ba za su taba karb'a na ba har Abada. Mun zo ta sha ana kiran sallar mangariba ammh ban damu ba gwara komai zai Faru dani ya faru da ni a hanya, da na bari ya faru da ni a gidan su Assadiq. Allah ya taimakeni na samu motar da ta taso daga Sokoto ta sauke wasu mutane a gusai, shi ne ma samu na shiga muka tashi da wuri, muna tafe ina bayan mota na Rufe rabin Fuskata da mayafi ina ta kuka ni kad'ai kamar raina zai fita ba kuma kukan kome na ke yi ba sai na Soyayyar Assadiq da Tunanin yadda Rayuwata zata kare in dan babu Assadiq a cikinta. Wayata ta dawo dani hayyacina, ina Dubawa naga Saliha ke kirana Sai na kasa Dauka saboda bansan me zan gayamata ba. Sai da ta yanke sannan na samu Damar Tura mata sakon ta yi hakuri mijina ya kirani yace bai amince na kara kwana ba, shiyasa na tafi ban mata sallama ba ammh ta yi hakuri. Ina Tura mata sakon sai na yi kokarin kashe wayar gabadaya. Sai ga kiran ASSADIQ ba kakkautawa, da ta katse kafin na kashe wayar sai wani kiran ya shigo, sai kawai na maida wayar jaka na Tusa kaina a Tsakanin Cinyoyina ina kuka. Har muka isa zariya ina jin karan wayata a jaka tana virabtion daman Tun jiya na sakata a silent. Motar ta yi gudu gaskiya wajen tara da wani abu muna zariya. Daga tasha na samu mashin sai gida, kowa ya kwanta anguwan ma tsit kamar ba Mutane. Na lalubo key din dakina a jaka na Bude kofa na shiga, nan falo na watsar da komai na kwanta a kasan Tayels ina kuka kamar wata karamar yarinya. Halin da ni ke yasa na manta da cikina, sai chan da naji yunwa na mukurkusana na mike na saka Ruwan zafi na sha tea, sannan na Diba na yi wanka na Dauro alwala na Rama Sallar mangariba da Isha'in da suka Kubcemin. A daran na kwana kuka da neman mafita daga karshe na bi shawaran Tahir na yin nesa da Rayuwar Assadiq a wannan Lokacin. Na yi tunanin naje gidan Adda Fati sai kuma na fasa ta inda aka hau ta nan ya kamata a sauka. Tun safe na tashi na fara had'a kayana acikin akwatuna, ina kallon kayan Assadiq ina kuka, ina kallon dakin ina Tuna Momemt din da muka yi tare cikin Farinciki. Wata zuciyar tace karatun ki fa? Sai ma kara gayama kaina Tunda na Rabu da wanda ya yi min sanadin karatun to miye amfanin karatun a wajena? Babu ya zama Dole na tafi tun kafin abubuwa su zo su faru ba daidai ba. Sai da na gama had'a kaya na duka, na yi tunanin zan tafi da su na bar wasu, sanda na Dauko wayata Assadiq ya kirani yafi sau arba'in sannan ga sakon sa nan na magiyan na Daga wayarsa na kuma Sauraresa. Ban bi ta kansa ba Sakon Saliha kawai na Bude ta nuna bata ji dadin na tafi ban yi mata sallama ba. Sai kuma kiran Safiya Ahmad kila mganar makaranta ne, itama ban bi bayanta ba na kashe wayar gabadaya na turata a cikin jaka. Ban so na kara kwana a garin zariya ba, a niyyata sai a wajen Amma naje na gayamata garejin da ta yi ko nace kuskuren da Soyayyar da ta ke min yau ga abunda hakan ya janyomin. Sai dai me? Ciwon kai ya matsamin daman Tunda na tashi da shi na tashi sai ban bi ta kai ba tunda daman na kwana kuka daman na yi Tunanin haka zai faru. Ina ta karfin hali had'a kayana da kauda wasu, sai kuma zazzabi ya Rufeni, na had'a tea domin na sha Tunda ba ni da kuzarin dafa abinci sai amai komai da naci tundaga jiya sai da na Amayar da shi ba komai acikina sai Kakarim Aman na ke yi ba abunda ke fita acikin cikina. Wasa wasa kafin Dare zazzabi da kasala da Ciwon kai ya kwantar da ni, sai taruwan miyau a bakina, jikina har ya saki ko sallah sai dai na yi a zaune, haka na kwana na yini cikin wannan Halin su Maman suhailat kuma ba su san dawowata ba, balle su lekani su gani kuma tunda na Dawo ban fita ba, sannan kofata na kulle. Ba na iya cin komai sai Ruwa shima da naci zan yi amansa, ranar talata da naga zan mutu ne na had'a tea da Ruwan sanyi na sha a falo na yi amansa ban iya tashi naje Tiolet ba. Jikina gabadaya ya saki duk na Rame sai Idanuwana da baki da Hanci daman gashi komai nawa karami ne ballatana ya had'e da cuta. Ranar Laraba ina falo kwance saman Tayels kamar ruwa ina maida Numfaashi naji muryan Safiya suna mgana da Ummi. Ta na ce mata kamar ba na nan fa, na yi tafiya, Safiyan na fadin ta yi ta kiran wayata a kashe. Gani na yi in na bari Safiya ta bar gidan nan zan mutu acikin Daki ba wanda ya sani. Da Rarrafe na Rarrafo har kofar daki na Bude lokacin har Safiya ta juya zata tafi, ita kuma Ummi daman da ta fito shanya ta koma Dakinta. Sai dai Safiya taji ina kiran sunanta cikin Dakushewar murya. Cikin mamaki da juyo ganina kwance a bakin kofar dakina ina maida numfashi yasa ta nufeni hankalinta tashe ta na kiran sunana. Cikin firgici tace"Hasiya me ya faru? Ba ki da lafiya ne? Ta na mgana ta na tab'a jikina da taji kamar wuta. Miyau na bin gefen bakina nace"Safiya ba ni da lafiya, komai baya zama a cikina sai na yi amansa kamar zan mutu." Safiya na jin haka ta taikamin na mike muka koma cikin Daki, ita ta Daukomim wata Riga na sauya duk da taga kayana a had'e bata damu ba tunda ance na yi tafiyqa kila na dawo kenan na fara rashin lafiya. Ta daukomin Hijabi da takalmi na saka ta tambayi jakata na nuna mata ta Dauko harda wayata a ciki, akwai Kudi a hannuna sannan ina da shi a banki, daman Akwai Atm aciki Tana Rirrikeni dani muka fito ita ta kulle Dakin nan muka had'u da maman Sulahait ta na ganina ta fara salati ta na fadin"Na shige su Hasiya daman kin dawo? Baki da lafiya ne naga kin dashe kin yi uban fari kamar wata mai yaron ciki? Ni dai halin da na ke ciki bai barni nayi mgana ba Safiya ce ke fad'amata na dawo kila Ciwon ya kwantar da ni, Sai ta Fara fad'an ana zaman makota kuma sai na yi shuru ban iya kiran kowa ba. To ni Allah na Tuba ina cikin wani yanayin da ba na iya gane komai ma da komai, Safiya na rikeni da ni muka fita bakin titi muka samu adaidaita, muka hau ta tambayeni wani asibiti muke zuwa nace mata ta kaini kowanne, sai tace muje asibitin musulmi akwai Cousin dinta na aiki a wajen, tun ma muna adaidaitan ta kira ta ta fad'amata sai tace mata tana asibitin sai mun zo. Saboda ita yasa muna zuwa ba Dadewa naga likita, ita ta yi mana shige da fitan siyan kati da Sauran su, likita na min Tambayoyi ina amsawa daganan ya turani dakin da za'a dibi jinina da Fitsari sannan yace na galabaita zasu Rikeni su gani zuwa yammah. Ni dai gani nan kwace kamar ruwa a wani office mai Dauke da karamin gado na marasa lafiya. An dibi jinina sannan Wata Nurse ta rakani Tiolet na yi fitsari a wani Roba sannan na dawo na kwanta Safiya da wannan yar'uwanta na ta ke ta Shiga ta fita a kaina har sai da aka sakamin Drip, abu d'aya ke damuna miyan bakina da baya yankewa, sai da Safiya ta sama min leda ina tofawa aciki, ko fa Barci na ke yi in miyan nan ya Taru sai na tashi na zubar da shi na ke samun sukuni. To yau din ma haka ya faru barci ya kwasheni ammh bi ni bi ni Miyan bakina ke tadani, kwata kwata na kasa gane kaina, zuwa yammah sai na samu karfin jikina sosai har Safiya ta fita bakin asibiti ta siyomin kayan marmarci naci, kuma tace ta Duba wayata ba Chaji balle ta gayama yan'uwana. Ni kuma sai nace ta kyalesu kawai tunda naji sauki, sai da ruwan ya kare na koma gaban likita, daman kananan Roba biyu aka sakamin sai babba guda daya. Abunda Likita ya fad'amin ya sandar dani, ya na mikamin Result din da suka gani acikin jinina da fitsarina, ammh na kasa karb'a saboda Tashin Hankali da mamaki. "Ciki gareni ni Hasiya, haka likita ke fad'amin har na Tsawon wattani biyu da kwanaki." Sannan ya Cigaba da bani shawarwarin cin abinci ko da zan yi amai sannan da samun cikakken Hutu da natsuwa, sai kuma yace ina da maleria a jikina sai na kiyaye, ya Rubutamin maganin karin jini na samu ciki sai paracetomol sai mganin Maleria. Na fito rike da Takarda a hannuna ina tafe miyau ya cika bakina, har mganar Miyan na yi masa yace na yi hakuri zan bari zuwa wani Lokaci, ammh yanzu na rika cin cingam ko shan minti. Safiya na ganin na fito ta zo ta rikeni muka samu waje muka zauna. Ta karbi takardun hannuna ta na fadin"Me likitan yace? Kai Tsaye nace"Ciki gareni Safiya." Sai ta washe baki ta na fad'in"Daman Sister Zainab ta fad'a tace ta na Tunanin ciki ne, kai Congratulation kawata na yi miki murna soon to be come a mother." Ta fad'a ta na dafa kafad'ata cikin murna sai kawai na bi ta da kallo ammh na kasa mgana sai dai na yi mata ya ke, takardan mganin ta Duba ni kuma sai na kalleta ina fad'in"Magunguna ne ya Rubutamin akwai sauran kudi a jakar ko? Sai tace"Akwai kudi ammh ba su da yawa 5k na gani kuma kinga an siya kati an biya kudin ganin likita sannan an Rubuta ruwa da alluran da aka yi miki." Ina Rausayar da kai nace"Akwai kudi a cikin bankina, ki yi amfani da Atm dina." Sai ta amsamin da Toh, kafin tace bari taje ta dawo. Nan ta barni ina zaune ina Tunanin, makomata, shin makomar Tafiya ko kuma makomar zama ne? Ina shafa cikina ina hawaye to in na tafi ina zan kai wannan gudan jinin da ke cikina? Ashe akwai rabo mai karfi a tsakanina da Assadiq, Shiyasa har aka gano wannan Implant din ajikina aka Ciremin shi Saboda wannan Rabon da zai Shiga Tsakanina da Assadiq. Lalle na kara Shiga cikin Tsaka mai wuya, ni dai bazan zubar da cikin jikina ba sanman bani da tabbacin Uban cikin zai karbesa Tunda tun asali baya so ya had'a zuru'a dani. Hango su Safiyq na yi da yar'uwanta yasa na yi goge hawayena har suka kariso. Congrarulation Sister dinta ta fara yi min, na amsa ina ya k'e, Safiya ta nuna min magungunar da ta siyo min ita kuma yar'uwata ta zauna gefena ta na bani shawarwarin yadda zan kula da kaina ina gyad'a mata kai. Sai shidda Saura muka bar asibitin muka koma gida, Safiya tamin kokari Daman ta jini shuru ne ban je makaranta kuma bata samu na a waya Shiyasa ta zo, ba ta tafi ba sai da tambayeni abunda zan ci nace ta dafamin shinkafa da mai da yaji ita na ke sha'awa. Sannan ta sakamin Ruwa na yi wanka naji karfin jikina, ta na nan maman Sulaihat ta shigo, ta na ganin ina tofar da Miyau a leda ta fara fad'in Allah ya inganta tun ballatana da taga Safiya na dariya sai ta san abunda ta ke zargi ne, gashi kuma rame na yi wani irin Fari fayau da ni. Safiya sai da tayi mangariba ta tafi, tace zata rika sakamin Attendence in kuma za'a yi test zatamin kafin naji sauki na dawo makaranta. A haka muka rabu bayan na yi mata godiya sosai. In da Allah ya taimakeni Maman Suhailat ke kula dani, zata shigo da Safe da rana sannan da yammah , tace me zan ci? Komai kuma nace ina so zataje dakinta ta dafamin, in ba ita ba yarta ta dafamin, ita kan zo ma tamin Share share ko ta sakamin ruwan wanka, Ummi dai ta shigo ta gaisheni ita da matar da ke dakin Fadila yanzu. Ina cin abinci ammh ba sosai ba, Sai dai abinci na daga Tuwo sai Fate , sai kuma Shasshaka na ke iya ci sai kuma Kunin tsamiya. Sai kuma kunzo saboda Miyan da na ke yi, ba domin maman suhailat ba da na zama kazama. Wayata kuma tundaga ranar ban kara kunnawa ba, ta mutu ma ba chaji Adda Fati ma ta ji ni shuru kuma wayata a kashe yasa ta aiko Habiba ta Dubani sai ta iskeni kwance ina Fama da Farin baki da miyau. Ta koma ta gayama Adda Fati sai gata tazo, ni da bakina ban fad'a mata ina da ciki ba ita ce ta gane, kuma itace ta gayama Ramatu da Adda Rukayya. Amma kanta Adda Fati ta kira ta ta na Fad'a mata ina ta fama da Laulayi. Ta kirani ta gaisheni har da hawayenta na Farinciki nima yau zan zama uwa, Ramatu da Adda Rukayya duk sun zo dubani. Abakin su naji na koma kamar Zabiya saboda hasken da na kara sannan dagani cikin nan zai sakani rama Sosai. Suna ta dai zencen su, Saboda ganin ba na iya komai yasa Adda Fati ta ce Habiba ta zauna da ni har sai na ji sauki na kama jikina, nace mata da ta bar shi Maman sulaihat ma na kula dani, sai tace sai a barta da Wahala? Har daki Adda Fati ta shiga ta yi mata godiya tace bakomai kamar y'a ta Daukeni. Wasa wasa sai da na kwashe kwana goma sha ina kwance sannan naji sauki na mike, sai dai ban daina kwana da zazzabi ba, sannan ga Miyau ni shi yafi damuna ba, haka zaka shiga cikin Jama'a ka na fama da Miyau? Sannan Tun naga nafi Sati Biyu Assadiq bai biyo bayana ba na kara Tabbatar da ma da kaina zama bai ganni ba. Duk a tunaninsu Adda Fati Assadiq ya zo ya dubani ya koma ne, ganin bani da matsalan komai yasa ba su kawo ma wani Tunani ba. Sati daya Habiba tamin nace ta koma gida naji sauki, ranar da na cika Sati biyu Ranar lahadi, daman a ranar na gama kudurin Tafiya wajen Amma Tunda naji sauki. Zama na ba shi da amfani , bazan taba Damuwa don Assadiq bai karbi Cikin jikina ba, ni dai ina son kaya na kuma zan renesa na haifesa ko da shi d'in baya bukatar haka. To ta ina zai bukaci haka Tunda ba Sultana bace? Ni fa daman taimako na ya yi, baya so na ban dace da Rayuwarsa ba shiyasa ba zai zo ya had'a wani abu da ni ba. Safiya ta dawo wajen sau biyu ta Dubani, ta yi ta min fad'an na kunna wayata sai na yi mata karyan inaga ta lalace tunda na yi ta kunnawa taki kawowa. Misalin karfe sha daya da wani na Safe ne, na yi wanka na shirya cikin Doguwar rigar abaya baka sai na saka Hijabi saboda na rame. Na adana komai Saboda bansan yadda Tafiyar tawa zata kasance ba, ammh ina ji a jikina ba ta dawowa bace. Na janyo akwatina babba da karamar sai karamar jakata da na saka Muhimman abubuwana, na yanke shawaran zan ce ma Maman suhailat cewa zan je wajen mafiyata Saboda Mijina sun tafi wani aiki kuma zai Dade bai dawo ba saboda gudun zargi. Da wannan shawaran na saka Takalmi na janyo akwatina kii sai kofar Daki na saka hannu na bude da makulli sannan na Cire makullin a Hannuna. Ina Bude kofar, ya na karisowa wajen kamar ko daman ya na wajen ne ni dai ban sani ba. Na dai gansa kaawai a gabana, ya na kallona nima ina kallonsa cikin mamakin ganinsa. ASSADIQ ne sanye da kananun kaya Riga da wando fari da baki sai jaket da jakar baya, duka Hannayensa na cikin Aljihun wandonsa. Yadda na ke kare masa kallo shima haka ya ke karemin kallo. Cikin mamakin ramar da na yi masa har a ido, ni kuma naga ya yi kiba sannan ya kara haske. Sai naji Duhu ya mamaye ganina na kishin Tuna amarci fa ya ke yi ai Dole naga ya sauya. Kawai sai na juya masa baya ina kokuwa da Numfashina. Mirmishin saman baki ya yi sannan ya taka ya shiga dakin ya na fadin"Tsanar da kika min siya har ta kai ki juya baya daga kallon Fuskata? Sai kuma ya bi akwatin gefena da kallo. Kafin ya yi mgana na koma falo Fuu, sai ya bi ni da kallo kafin ya Rufe kofar ya Tura akwatin ya taddani a falo a zaune a kasa na saka kaina a gwiwa. Da Sauri ya ijiye akwatina tsakar falo ya karisa gareni jikinsa na rawa ya ke fadin"Siya na san ni me laifi ne ammh don girman Allah ki tsaya ki Saurareni." A fusace na Dago ina kallonsa kafin nace"Na saurareka? Ashe akwai sauran abunda zaka gayamin wanda ban ji ba, ko kuma nace ban gani da idanuwana ba? Umh! Abubakar kenan" Na fad'a hawaye na kawo idanuwana, da Sauri ya saka Hannu zai rikeni na Zabura naja baya ina fadin"Kada ka kuskura ka tab'ani Tunda BAKA SO NA ASSADIQ." Ido ya zaro kafin yace"waye ya fad'a miki ba na son ki SIYA? Cikin Idanuwansa nace"Kai ne." Cikin karin mamaki yace"Ni kuma? Look Siya boye miki Asalina ya na da Nasaba da Sonki da na ke yi, ina sonki ba na son na Rabu da ke shiyasa ban taba fad'a miki komai game dani ba." Kallonsa na ke yi ina tsiyayan hawaye kafin na kira sunansa"Assadiq." Sai kawai yace da Sauri"Ki tsaya ki Fahimceni Siya, mu zauna mu yi mgana don Allah, ammh kafin nan wannan akaatin nan na miye ne? Ina kike shirin tafiya? Kai Tsaye nace"Wajen mahaifiyata." Sai ya koma ya zauna Dabas kafin yace"Why Siya? Sai ki iya tafiya yanzu ki bar ni? Mirmishin takaici na yi kafin na jawo karamar jakata, na bude na Dauko masa takardan shaidar cikina na mika masa. Sai ya ki karba'a ya na kallona Sai ya kira sunana "HASIYA.." Da Sauri nace"Sakon ka ne aciki ka Duba." Ba musu ya karb'a ya Bude ya Fara Dubawa, ina kure masa ido naga ya Dago a razane ya na kallona. Cikin mirmishi nace"Ka yi mamakin ko? Ka yi mamakin ya aka yi na samu ciki Ahalin ka kaini an datsemin Hanyar samin cikin ko Assadiq? Ina ganin Razana da Firgici a idanuwan Assadiq. Ya na kallona ina Hango kunya nadama da Tsananin tsoro da wani abu a akwayar idanuwansa. Cikin Sauri na mike ina fad'in"Zaka iya sakina Assadiq ammh sai dai ka sani ko Sama da kasa zata had'e bazan amince na zubar da wannan cikin ba." Na fad'a ina kokarin Danne kukana ammh sai da ya kwacemin. Cikim kuka na cigaba da fadin"Na yarda baka sona, ammh ni ina sonka Assadiq don Allah ka barni da cikin nan na yi maka alkwarin zan yi nesa da Duniyarka har abada ba wanda zai san ka na da wani gudun jini bayan Ya'yan da Sultana zata haifa maka." Ban karishe mganata ba naji ni gabadaya acikin jikinsa. Ya yi min wani karkarfan Riko cikin wani irin Sauti yace"Tare zamu rene gudan jinin mu siya, zai kuma zo Duniya ya iske gatan Iyayensa Biyu tare da gatan duka Ahalim mu Siya." Cikin mamaki na Dago fuskata da tayi jage jage da majina ina kallonsa Cikin mamaki na kira sunanshi. "Assadiq" Kai ya gyad'amin kafin yace" Ina sonki HASIYA, ki yarda ko karki Yarda, ina sonki sannan kuma na yarda da kuskurena na kuma karbi laifina zan kuma gyara, ta hanyar gayama Ahalina da Duniya cewa ke MATATA CE.! Kuma cikin da ke jikin na wa ne" Ya fad'a ya na shafa kasan marata, sai naji kamar zan suma saboda dad'i Cikin kuka nace"Ko da kuwa hakan zai jefa rayuwarka cikin Tsaka mai wuya? Da sauri yace"Eh na amince da hakan matukar zan cigaba da kasancewa tare da ke na shirya karban komai Siya." Bansan lokacin da na kara Rumgumesa ba ina dariya ina kuka nace"Nagode Assadiq. nagode." Kwata kwata naji jin haushinsa ya fita daga raina daman Fargaba na d'aya shine yace zai sakeni ko zai rabani da Cikin jikina. Sannan maganar Boyemin Asalinsa da ya yi bai dameni ba, ta wanni Fanni ya yi hakane domin amfanin kaina da na shi gabadaya. Ni ban damu da ya so ni ba, ni dai ina son shi kuma ina fatan na zauna da shi har karshen rayuwata. *Janafty* *TMWBK302* *TMW is a paid Novel, Pay 500 for regular or VIP N1K, Via 0552179550 Jamila Umar Gt bank, 09069067488* https://chat.whatsapp.com/I7uxPXgtPKBHnVQjaEbRlE Mun dad'e tsaye Rumgume da juna kafin ya sake ni, sannan ya bi fuskata tare da bakina da sumbata mai yawa. Sannan ya ja hannuna muka zauna saman daya daga cikin kujerun falon. Ya Rumgumoni ta rabin jikinsa na Dama, lokaci daya hannunsa na shafa kasan marata cikin sannu a Hankali kamar ya na shafa kwai. Ni kuma na lafe a jikinsa ina sauke Numfashi ji na ke yi kamar dukkan wasu matsalolina na nan duniya sun kauce, kamar ni kad'ai ce Sarauniya da ta yi saura a duniya. Idanuwana suna lumshe naji Assadiq ya fara mgana cikin Taushin murya da fari da kiran sunana ya fara "HASIYA." Na amsa cikin Dakushewar murya da alamun sanyi a cikinta, miyau kuma ya fara taruwa a bakina na kira sunansa nima bayan na amsa kiransa. "Na'am Assadiq din Hasiya" Mirmishi ya yi domin har sai da kunnuwana suka jiyomin Sautin mirmishin nasa da ya shiga har cikin zuciyata. Cikin kwantar da kansa saman kaina ya fara fad'in"Zan fada miki ko ni waye, sannan zan amsa duka tambayoyinki game dani, nasan zaki ce me ya rage baki sani ba? To har yanzu akwai muhimman abubuwan da ya kamata ki sani game da Rayuwata Siya, ammh kafin nan sai kin fad'amin meyasa a wanchan Ranar a gusau kika taho zariya cikin Daran nan Siya? Sannan me yasa kika ki Daukan Wayata? Daga karshe sai naji ta a kashe, Siya kinsan iya adadin Tashin hankalin da na shiga bayan tafuyarki kuwa? Kinsan adadin irin Bugun zuciyar da na rika fama da shi in na Tuna a yanayin da kika taho zariya da daddare sannan ga hanyarmu sai a hankali? Me yasa kika yi haka? Ajiyar rai na sauke, kafin na Dago kaina miyau ya cika bakina shiyasa na tashi da sauri sai ya rikoni ya na fad'in"Ina kuma zaki muna mgana? Bakina na nuna masa da ya cika da Miyau sai ya yi saurin sakina ya na fad'in"Sorry." Kai na gyad'a masa, sannan na wuce zuwa cikin daki na shiga makewayi na zubar da miyan bakina sannan na wanke bakin, ban fito ba sai da na samu wata bakar leda na taho da ita, gudun kada maganar ta Gundiremu da yawan tashi na. Sanda na dawo gefensa na sake zama kamar dazu sai ya kara rumgumoni,Ya dora kansa saman kaina da ke gefen wuyansa, ni kuma sai na nuna masa ledan hannuna ina Fad'in"Ka yi hakuri, na zama kazama yanzu ban iya hadiyan miyau." Mirmishi ya yi kafin yace"Mun zama kazamai zaki ce, ni ma in naji miyan sai na Tofa abuna aciki ko? Ya fad'a ya na leken fuskata sai na kyalkyace da dariya shima ya na tayani. Sai da muka natsu sannan ya kalleni ya na fad'in"Umh baki bani amsar tambayoyina ba? Shuru na yi kafin nace"Tsoro na ke ji, ba na so na zauna wata acikin yan'uwanka su Fahimci alakarmu da kai wani abu mara dadi yazo ya faru shiyasa na tafi." Na kasa fad'a masa karona da abokinsa saboda bansan ya zai Dauki mganar ba. Kai Tsaye yace"Me yasa kika tafi? Ba wajen Saliha kika zo ba? Ba wanda zai fahimci wani abu tunda ki na da alaqa da Mijin da Salima ta aura." Cikin mamaki na kallesa shima ni ya ke kallo kafin ya yi mirmishi yace"Kin yi mamakin ya a ka yi duk na san wannan ko? Sai bayan tafiyarki a ranar nasan haka nima." Nan ya fara bani Labarin abunda ya faru bayan tafiyata, ashe yan'uwansa sun hanashi sakewa su dai sai an yi Hotuna, in kuma ya nuna wani abu za su iya gane akwai wani abu a kasa. Ya na fad'in sai bayan mangriba suka sake shi daga Daukan Hotunan nan shima din ya Tuburene yace zai je ya yi sallah. Ya na gayamin hankalinsa tashe ya rika nema na acikin gidan nan bai ganni ba, sannan ga shi ya na kiran wayata ba na dauka, yace har Tahir ya tambaya tunda ya sanni, ammh yace bai ga fita ta ba, ban yi mamaki ba Tunda nasan abokinsa ba ya son alakarmu ba abun mamaki ba ne in bai gayamasa mganganun da ya fad'amin ba. Yana cikin nema ne, yaji Saliha na cigiyar kawarta da ta zo mata biki daga Zariya, sunanta kuma Hasiya, daganan sai ya sha jinin jikinsa, ya tabbatar ne lokacin da yace in Saliha na da Hotona ta nuna masa sai ko ta nuna masa ya ganni, itace ma ta ke fad'a masa cewa ni yar uwar mijin Salima ce daga zariya. Ya na gayamin Hankalinsa bai kwanta  ba, sai da yaji Saliha na fad'in na yi mata Sako nace mijina ne yace na Dawo gida, Tun kafin ma nayi masa tambayar da ke cin raina naji ya na amsamin. Assadiq ya kalleni cikin sanyin murya ya na fad'in"Nasan zaki ce meyasa bayan haka ban biyo bayan ki ba? Siya bani da mafita illah zabin na zauna a gusai tare da Sultana da ta tare a gidan da Abba yaa bani tun a daran, in na yi wani motsi abubuwa za su kwabe ni kuma bazan so haka ba, Shiyasa na zauna har na Tsawon Hutun da na Dauka na Sati daya daga wajen aiki, ammh na rantse da Allah ki sani ko wata dakika ba ta wuceni sai na Tuna ki Siya, wayarki ta na kashe, sannan karamar wayata ta bace a sha'anin nan na rasa duka Lambobin su Adda Ballatana na kira su naji Lafiyan ki, sai dai ina da yakinin guda daya da cewa kina lafiya, na tabbata da wani abu mara dad'i ya sameki da zan samu labari, da wannan Tunanin na samu kwanciyar Hankalin komawa wajen aikina sai dai tare da Nadama mai Dimbin yawa da kuma alkwarin zuwa na same ki na baki hakuri, sannan na gayamiki komai game dani, kuma ki tambaayeni abunda baki sani ba na amsa miki." Shuru ya biyo bayan maganarsa kowa da abunda ya ke tunani, ni ina Tunanin wannan Satin dayan da ya yi tare da Sultana amarci suka sha? Kamar sai naji idanuwana sun ciko da kwallah, kishi Halitta ne ina son Assadiq, kuma nasan Sultana itace zab'insa da zabin Danginsa Dole zan ji ciwon abun in dai na tuna ko da Sunanta ne. Shi ko Sadiq a cikin ransa ya ke wani Tunani, Hasiya itace matarsa ta farko, kuma ya aureta ba'a a matsayin budurwa ba, Sultana kuma Budurwace, Zai iya ba da shedar shi ya fara saninta a y'a mace, akwai wani sirri da dukkansu suke da shi, sannan kuma sirrin na su ya yi tasiri mai girma a tsakaninsa da su, ya bar ma ransa Muhimmanci da kowaccensu ta ke da shi a Rayuwarsa, ya na son Siya, kuma ya na son Sultana ba ya kinta, Shiyasa komai zai faru bazai Rabu da d'aya Saboda D'aya ba. Kamar daga sama ya ji na jefo masa tambayar yanzu shi daga ina ya ke? Naga kuma wannan karon bai zo da mota ba? Assadiq ba shi da wani zabi illah na Boye wata gaskiyar domin ya kara gina wata gaskiyar. Sai kawai yace daga Abuja ya ke, alhalin Daga Gusau ya ke, tun ranar jumma'a ya isa da yammah, ya gaji da tuki ne sai kawai ya hau ta haya, tunda ya tafi sultana ke damunsa a waya da Shagwabar ta yi kewarsa ita dai ya dawo ta gansa, daman dakyar ta barshi ya tafi, ta na ta kukan wai bata warke ba zai tafi ya barta. Duk da yasan ba wani Rauni ya yi mata Sosai ai shi ba karamin mutum ba ne yasan mace, ya bi da ita a Hankali sai dai yasan yan'uwansa ne suka sakata ta yi ta shaye shayen magungunar da ya sa ya makalemata a satin da suka yi armaci ba karya ta Gurzu a hannunsa shiyasa ya ke Tausayinta, kuma ya kasa kwabe shagwabarta a garesa, duk da yaso a wannan satin ya zo yaga Hasiya. Ba shi da mafita sai ta fara zuwa Gusai yaje yaga Sultana, itama ba domin Hasiya na ransa ba zata iya Rinjayansa ya koma Abuja batare da yazo Zariya ba. Haka suka rabu ta na kukan shagwaba, duk da ta na kusa da gida, kuma in baya nan Siyama ke zuwa ta na tayata kwana. Ga shi ta koma makaranta so ba ta da wani kadaici tare da ita, kawai Sakalci ne da Shagwaba na yaran zamani. Ba na son mganar Sultana Shiyasa na kauda maganarta a tsakanim mu cikin Sanyin murya nace"Tambayata itace me yasa tun farko ka yi mana karya baka da kowa sai kakar ka? Mirmishi ya yi kafin yace"Bansani ba, nima kawai naji ina fad'a ma Amma hakane, sai dai daman duk wanda ya had'u da ni ba lalle ba ne kafin mu rabu ya san wani abu game dani ba, ina bambamta Rayuwata ta gida da kuma Rayuwata ta waje." Dagowa na yi ina kallonsa kafin nace"Kowa na sonka a gidan ku, sannan naji ana kiranka da wani suna ko magajin gari ko? Dariya ya yi kafin yace"Magajin gida ne Sunan Siya? Kina so kinsan waye mijin ki? Sai na gyad'a masa, kai tsaye ya maida kaina saman kirjinsa ya kara gyaramin zama sannan ya shiga bani Labarinsa haihuwarsa karatunsa Asalinsa da komai da komai yawan yan'uwansa mata, gatan da ya ke da shi Soyayyar da Mahaifinsa da kakarsa su ke yi masa da Dalilin da yasa a ke kiransa Magajin gida, da kuma labarin wacece sultana? Alkwarin auran da ke tsakaninsu tun tana yarinyarta da alakarsu. Ya karishe da fad'in"Ni a gida mu ba bu da'n gata irina, ni kad'ai ne namiji sauran yayyena duka mata ne, kanwata guda d'ayace Autarmu Siyama, Sai Sultana da ita daman alkwarin aure ne Tsakanina da ita, Ina daraja mata guda Biyu a Rayuwata mahaifiyata da kakata bani da kamarsu, Abba ba shi da wata Damuwa ya ma fi fifita Ra'ayina akan na shi Ra'ayin, Siya ina jin wani nauyin acikin zuciyata nauyin cin Amanar yardansu da na yi, na aure ki batare da sanin su ba." Ya dakata lokaci d'aya ya na sauke Numfashi, ni kuma ina jikinsa nace"To me yasa ka aureni in dai baka sona? Kuma me yasa ka aureni ba tare da sanin iyayenka ba? Cikin Wani irin yanayi yace"Bansani ba Siya, abu daya na sani naji Tausayin Amma sosai, kuma naji Rauni ya shigeni da naji Labarinki, maganar gaskiya ba so ba ne yasa na aureki Tausayi ne, ammh daga baya sai na Fahimci shi So dabam ya na iya Farawa da Tausayi sai ya Rikide ya koma Soyayya  Allah ne shaidata Hasiya, Ina sonki kuma ina kaunarki kuma ina son na Dauwama tare da ke har Abada, in da ba na sonki a yadda na ke cikin Tsaka mai wuyar nan da Tuni na Rabu da ke., Maganar kuma meyasa na aureki ban sanar da Ahalina ba? Ina da dalilaina na Farko bani da Lokaci, na Biyu kuma in har na je musu da maganar ina da yakinin ba za su amince ba, ko da ma Abba ya Amince Umma da Innani ba za su amimce ba, sannan a lokacin na yi niyar na sakeki bayan na baki jari mai Tsoka, shikenan in na bar zariya na koma gida komai ya kare, ashe ba haka ba ne, Allah bai aura ma na juna Domin mu rabu ba, saboda ke na rika Dojema auran Sultana har na Tsawon shekara uku, saboda ke na fara masters a zariya sannan kuma ke ce Dalilina na karb'an aikin kamfanin da na yi Bautar kasa a zariya  Siya kin Sauya Rayuwata, Saboda ke na zama mai karya kuma na iyata, Saboda ke ma ke wata Boyayyiyar Rayuwar da na san Cin Amana ce ga Ahalina." Ya na mgana ina jin zuciyata na kara narkewa cikin soyayyarsa, ina jin na gama yarda da shi, ko da baya so na to ina da matsayi mai girma acikin Rayuwarsa. Abu daya na ke so na kara sani, shine me yasa ya kaini aka sakamin Implanta?  Tunda yace ya na sona meyasa ba ya son had'a zuru'a dani? Kai Tsaye ya Dago ni muna kallon juna, sumbata ya ke shirin yi na yi saurin kauda kaina ina nuna masa bakina da ya fara cika da miyau. Sai ya yi dariya ya mikamin ledan da har miyau ya fara taruwa ya taramin na Zuba, ina kallonsa ya ijiye ledan a gefensa ko kyamkyami ba shi da shi. Cikin mamaki nace"Baka kyamkyamin Miyau Assadiq? Cikin sauri yace"Ina da kyamkyami mana, Sai dai ke ce ban isa na yi kyamkyamin ki ba, abunda ke sakaki miyan ai ni ne na Digasa ko? Zai sake rikoni na yi saurin kwace kaina ina fad'in"Ka bari na wanke bakina." Ya na dagamin gir yace'To miye? Ban kulasa ba na shige ciki da gudu sai da na sake yin brush sannan na dawo, kuma bai yarda ba sai da ya kama Fuskata muka sumbaci bakin juna na wani lokaci sannan ya kalleni ido cikin yace"Siya soyayyarki ce taja min duk abunda na zama yanzu, Wallahi kin ji Rantsuwan musulmi ban taba kyamatar komai da zai Fito daga Tsatson ki ba Hasiya, a lokacin bani da mafita ne, sai ta hakan dalilina shine ba na so ki samu ciki har ki haihu iyayena ba su san da ke ba, ba na so abunda zamu haifa ya zo ya Fuskanci laifin da ba shi ya aikata ba, Daman ina da niyar in komai ya Daidaita na gaya miki da kaina sannan na kai ki a cire miki, ammh har ga Allah har acikin zuciyata Siya bani da wata manufa ta sharri ko kin had'a zuru'a da ke daga bangarena." Ya karishe fad'a ya na kallona nima shi na ke kallo ammh na kasa mgana. Zuciyata daga chan gefen ta na gasgasta shi, wata kuma na Kokarin nuna min ba haka ba ne. Ganin haka yasa ya kara rike Hannayena ya na fad'in"Ki yarda dani Hasiya wlh ba karya na ke fad'a miki ba, ki Fahimceni." Sai na lumshe ido kafin na bude ina kallon yadda ya marairaicemin kamar wani maraya, lokaci daya kuma ya na shafa Tafin hannuna cikin wani irin Salon da ya sa, sai da tsikar jikina ya tashi. Bani da zabi illah Aminta da Assadiq domin nan duniya bani da wanda ya fisa cikin gyad'a kai nace"Na Aminta da kai Assadiq, na kuma Fahimceka na kuma yarda cewa baka na gudun had'a zuru'a dani saboda Canfi da ke kaina ba ne" Da Sauri yace"Astagafurullah.! Kada ma ki kara wannan Tunanin, ni ban yarda da Canfi ba , sannan ina da ilimin addini nasan Allah ke yi ba Mutum ba." Sai na yi masa mirmishi ina jin zuciyata na samun natsuwa kafin na koma saman kirjinsa na kwanta ina Fadin"Assadiq ya kamata ka yi saurin sanar da iyayenka mganata kafin na haihu ko? Ya na shafa kaina zuwa bayana yace"In sha Allahu, zan sanar da su kada ki damu." Sai na jinjina masa kai shuru muka yi kafin ya muskuta ya na fadin"Daman Alhaji Jibril baffan ku ne Siya? Sai na Dago ina kallonsa kafin nace"Na kaduna? Sai ya gyadamin kai, cikin mele baki nace"Eh kanin babanmu ne, ammh da ya ke sanadina yasa tunda babanmu ya rasu ba su duba bayansa ba, a cewarsu duk wanda ya rabemu shima zai iya rasa komai na shi." Shuru ya yi kafin yace"Mutane yanzu sun saki Allah sun kama boka da mallam, da kuma Canfe canfan banza da wofi, mutane ba ikilasi ba Tauhidi, sun manta da Allah shi ne Allah, komai baya faruwa sai da cewarsa da kuma Umarninsa." Ina jikinsa har a Lokacin idanuwana suka kawo kwallah kafin nace"Farkon Rayuwata na taso cikin Farinciki, Daga baya ta juye zuwa kunci da bakinciki na shiga Tsaka mai wuyar da kai ne ka fitar da ni acikinsa Assadiq don Allah ko da iyayenka ba su karbeni daga Farko ba, kada ka Juyamana Baya ni da cikin da ke jikina." Sai kawai na fashe masa da kuka ina Rokon kada ya zabi sultana ya rabu dani kai tsaye yace"Kamar yadda Saboda ke ban barta ba, ke ma kuma saboda ita bazan barki ba Siya". Sai na kara kamkamesa ina ta kuka, shi kuma ya na aikin lallashina. Daganan kuma daga lallashi sai kuma ya fara kokarin nuna min yadda ya yi kewata. A nan saman kujera mun kasa ko shiga ciki komai ya wakana, ni kaina nasan na yi kewar mijina, shima haka ballatana ga cikin jiki, Sai dai muna Samun natsuwa na mike da gudu sai Tiolet naje zubar da miyau shi na bari da tattara mana kayanmu, ni daga nan tubewa na yi na tsabtace jikina. Ko da na fito ya shigomin da akwatuna ciki tare kayanmu da muka yi falati da su, shima wanka ya shiga ya Tsabtace jikinsa. Dagani har shi ba ma jin yunwa, nad'ewa muka yi a gado muna sake Sabon Hira ya kashe wayarsa gabadaya Saboda yace yanzu lokacina ne. Muna kwance a kan filo daya fuskokin mu na kallon Rufin Dakin, hannayemmu sarke a waje d'aya, Juyawa na yi na rab'i da rabin jikinsa na kira sunansa"Assadiq? Da sauri yace"Uhm SiyaAssadiq." Ina shafa gemunsa nace"Ya ku ka kare kai da abokin ka din nan? Domin nasan yasan har yanzu muna tare.? Assadiq ya yi shuru saboda baya so Hasiya tasan a kanta sukayi fad'an da ba su taba yi da Tahir. Sun rabu zukata ba bu dadi kuma Daga Lokacin ba su kara neman juna a waya ba. Ba kuma wani abu ya had'a su ba, sai Tahir da ya ke jifan Hasiya da kalmar Annoba sannan ya na rainata Saboda ita bazawara ce, kuma ya na kokarin nuna masa ya saka Rayuwar Ahalinsa a bala'i tunda ya kasa rabuwa da Hasiya. Yasan ya yi kuskure da ya yi masa karya ammh Hasiya matarsa ce kuma Sirrinsa bazai taba bari wani ya ci zarafinta ba Shiyasa ya yi ma Tahir Tsawa akan kada ya kara aibata matarsa in kuma ya kara sai ransa ya baci, shikenan Tahir yace yaje tunda ya zabi hasiya sama da shi, ya bar shi duk sanda ya gane kuskurensa ko ta kwabemasa yasan zai nemesa. Shima a lokacin ransa ya baci shiyasa har yanzu bai ko nemesa ko ta waya ba. Sai da yaji muryata ina kara fad'in"Uhm ka yi shuru? Da Sauri yace'Na fad'a masa gaskiyan cewa muna tare yanzu." Kai Tsaye nace"To me ya ce maka? Ajiyar rai ya sauke kafin yace"Me kuwa? Abokina ne fa ba Ubana ba Hasiya, ba shi da ikon zab'a min Ra'ayina" Sai na yi shuru na kasa mgana,Ammh na Fahimci shi da abokin nasa ba su yi Rabuwar dad'i ba. Gudun kara Tabarb'arewan al'amarin yasa na yi shuru da bakina. Sai dai na kara lafewa a jikinsa ina fad'in"To ka na Tunanin a yanzu bazai gayama kowa ba? Sadiq yace"Da zai fad'a da Tuntuni ysa fad'a, nasan Tahir bazai taba fad'an komai a kan ki ba, sai dai in dan ni ne na Bukaci hakan." Ajiyar rai na sauke kafin nace"Allah yasa komai ya zo da Sauki Assadiq." Cikin jinjina kai yace"In sha Allahu Khairan Siya ta." Daga haka ya Rumgumeni yace mu yi barci ya gaji, kamar wasa sai ga shi barci ya kwashemu dagani har shi, sai dai ni miyau ne ya rika tadani da na mike daman ya san miyau ne ya cika bakina. Muryansa cikin barci yace"Miyan nan ba shi da magani ne Siya? Ina kara kwanciya ajikinsa nace"Likita yace for now dai babu, ammh yace zuwa gaba zai rage." Kara rikeni ya yi cikin barci barci yace"Ya na takura min mata ne Shiyasa." Sai bayan azahar muka tashi muka yi sallar, shi ya fita ya siyo mana abinci da kayan marmari, ni kayan fruit din kadai na sha  suma ba'a wanye lafiya ba na yi ta amai, ya hadamin Tea shima na sha na yi amai, Tuwo nace ina so yaje ya siyomin Tuwon Semo miyar karkashi shi naci ya zauna a cikina. Duk wasu kayan kwalama sun daina Burgeni, Da daddare kuma Tuwon shinkafa ya siyomin miyar kubewa da ganda, sanda naci lafiyata kalau ammh kwana na yi ina ta faman Amai da miyan yanzu ya yi yawa, shi Assadiq yadda na ke ta bushewa ne damuwarsa da kuma Aman da na ke yi yasa da Safe ya tasani gaba muka koma asibiti ganin Likita. Bai yarda ba sai da likita ya karanta masa sai hakuri in cikin ya fara girma duk zan daina Aman sannan miyan zai Ragu, Ramar da na ke yi kuma kila Sanadin cikin ne, ammh zuwa gaba in na fara cin abinci sosai zan maida jikina. Bai bamu komai ba, sai magungunan karin jini na masu ciki ya sake Rubamin, Yace maleria ya rabu dani zazzabin dare da na ke yi cikin ne ya na Tunanin in ya yi kwari duk zan dawo Normal. Haka muka koma gida, ina kwance jiya da yazo da karfin jikina ammh washegari sai na kwanta kamar ruwa, kuma gashi gobe da Safe zai koma wajen aiki, maganarsa shine bazai barni ni kadai ba, gwara na koma gidan Adda Fati na zauna ko kuma Habiba tazo ta zauna dani. Ni kaina ina son na Huta sai nace zan je gidan Adda Fati na yi ko sati ne daga baya in zan dawo sai na Dawo da Habiba. Ga makaranta ma, da ya ke ya kunna min wayata, Safiya ta kira mun yi mgana tace an fara Test ya kamata na zo makaranta, shi kuma yace komai sai da lafiya na bari ko an wuceni na yi Difaring ni ko ina zan bari Yan ajinmu su yi gaba su barni. Da kansa ya had'amin komai da zan bukata washegari da Safe sai da ya kaini gidan Adda Fati ya kuma barmin isassun kudi sannan ya hau Motar haya Zuwa Abuja. Ita kanta Adda Fati  taji dadin haka Tun ballatana irin ramar da ta ga na yi, sannan taga laulayin nawa mai zafi ne. Tunda Assadiq ya tafi a rana ban san adadin sau nawa ya ke kirana yaji lafiyata ni da Baby ba, kullum cikin cewa ya ke da naji wani abu na koma asibiti, ni kenan kullum tuwo da tsaki, Komai baya min dadi, kuma ban daina amai ba ga miyau, maganar gaskiya ina Laulayi mai zafi sosai. Sati daya na yi gidan Adda Fati ta had'ani da Habiba muka dawo daganan Wajena ta ke zuwa makaranta. Bayan tafiyar Assadiq sai da na yi sati Biyu sannan na fara farfadowa, na rage Amai sannan na daina zazzabin dare, kuma yanzu zan ci abinci ya tsayamin acikina na wani lokaci a satin ya baro Abuja bisa adalci ya sauka a gusai, ya gayamin ban nuna wani abu ba, Tunda itama matarsa ce kamar yadda na ke da Hakki a kansa itama ta na da Hakki a kansa. Bai zo zariya ba sai da ya koma Abuja sai weekend Ranar jumma'a ya zo ya ganni, ranar da yazo Habiba ta koma gidan Adda shi kuma ya cigaba da kula dani. Duk da dai naji sauki sosai, ni kuma na matsa masa ranar litini da ya tafi da Safe ni kuma na Shirya na koma makaranta naje na iske Uban Assigemt sannan an yi abubuwa da dama ba na nan, Sai dai Thanks to Safiya duk ta min wasu abubuwan sannan komawata ta na kokarin koyamin abunda ya wuceni. Kullum da minti da cingam na ke yawo a jakata ko da kunzo Saboda Miyan bakina, ina shiga cikin jama'a akwai cutarwa saboda wani ya na da kyankyami. Ramewa kawai na ke yi, sai dai na fara cikar Fuska dagani In ji Adda zan yi girman ciki mai kumburi Domin tun cikina na wata uku da wani abu ya bayyana ajikina, ga shi dai ina da Tsawo ammh Tsawo na bai shanye girman cikina ba, in na saka Hijabi in ban saka hannu na kare ba sai ya bayyana. Ni da kaina na rage huld'a da Saliha, tunda itama taga ta na bi na ina basar da ita sai taja baya, duk da Assadiq yace mu cigaba da mu'amalan ba karya ba ne ni matar kaninta ne, ammh ni ce a karan kaina na kasa, sai na ke ganin kamar za'a samu matsala. Ammh lokaci bayan lokaci mu kan gaisa ta waya ko ta chart. Assadiq ya raba mana kwana ni da Sultana Tunda dukkanmu ba ma zaune waje daya da shi, sai yace duk bayan sati biyu zai fara zuwa ya sauka wajena, in ya koma ya yi sati daya, satin sama kuma sai ya sauka Wajen Sultana haka ya raba mana Tsarin kuma na amimce tunda sai da ya yi shawara da ni. A koda yaushe in na yi masa maganar Lokaci fa na kurewa yasan hanyar da zai fad'ama su Umma game dani sai yace na kara masa lokaci har yanzu yana Tunanin ta wacce hanya zai saukaka Lamarin, ni kuma gani na yi cikina na kara girma ina Tsoron nan gaba abubuwa su kara Tsami. Shi kuma Sadiq ya buga duka Hanyoyin samun mafitan ya kasa samu ne, kunya da wani irin nadama sun gama dabaibayeshi. Ba zai iya taran su Umma da mganar ya auri wata matar shekaru uku da wattani batare da sanin su ba. Ya zauna ya yi tunanin duk ya kasa samun mafita, Kuma ga shi ba abokin shawara, Tahir ne kuma yanzu yaja baya da shi ranar dai ya kirasa ammah a Dakile Tahir ya rika amsa masa shiyasa shima ya fita batunsa. Tunanin abun yasa har rama ya fara rashin natsuwa ta fara bayyana masa a fuska. A cikin irin Tunanin da ya ke yi sai ya yi tunanin Big sis Surayya, duk cikin yan'uwansa ya fi shakuwa da ita, kuma ya na mata kyakyawan zaton zata Fahimcesa, da yakinin zuwa ya gayamata abunda ya faru yaje gusai a satin, sun had'u a gida yace mata zai zo wajenta akwai mganar da za su yi, tace sai yazo anan ma agaban su Umma tace duk ya rame da Farko dai ya fara kiban Amarci. Mama na wajen tace wahalan zirga zirga ce na jeka ka dawo, Umma ta yi karaf tace sultana na gama makaranta ya sama mata muhalli ta bisa chan sai dai bayan wattani in sunzo ganinsu. Shi ko har ga Allah baya so Sultana ta bishi Abuja in hakan ya faru Hasiya fa? Kuma ga shi kad'an ya rage ya gama Masters dinsa shiga zariya zai yi masa Wahala  gaskiya. Ana gobe zai koma Abuja ya shirya da Daddare da niyar tafiya gidan Surayya  ai Sultana na ganin zai fita ta makale masa sai yaje da ita, ba shi da zabi ya sakata a gaba suka je. Duk yadda ya so ya yi mganar sai kuma yaji ya kasa, duk da Sultana ta ba su waje, ammh kuma guilt din abunda ya aikata yaki barinsa ya fad'ama Surayya komai sai kawai ya Bige da fad'amata in ya koma Abuja zai kirata a waya. Kuma da ya koma sai ya kasa kiranta tunda ya rasa ta ina zai fara, sai gaahi ta kira da kanta , ta na mai tuni kan maganar da ya ce za su yi kai tsaye yace in zai gayamata zai kirata da kansa, Daga baya ma data matsa masa sai yace mata bakomai. Ita kuma duk sai ta Damu, saboda tafi  kowa Sanin kanin na su ta tabbata akwai abunda ke damunsa. Har ta fara Tunanin ko sun samu matsala da Sultana ne? Ta shirya taje har gida ta turketa ta tambayeta Sultana ta rantse mata suna zaune lafiya cikin soyayya, daganan sai ta sare sai Tunaninta ya bata ko daga wajen aiki ne? Har megidamta ta yi ma mganar suka Tattauna shi yace koma menene kada ta matsa masa ta yi masa addu'a yadda ta ke da Sadiq ya tabbata da kansa zai zo ya fad'a mata da Damuwarsa. Da shawaransa ta yi amfani ta kyalesa sai dai ta dukufa yi ma kanin nata addu'an koma meke damunsa Allah ya kawo masa mafita ta alheri. Bata sani ba Allah ya amsa addu'arta sai dai kila mafitan ta yi jinkirin samuwa ko bayyana. A satin da zai je zariya wajen Hasiya ya samu wayar Umma cewa Innani ba ta da lafiya, ta zame ta fad'i acikin Falonta yanzu haka ta na asibiti. Hankali tashe ya kira Hasiya ya gayamata yace ta yi masa Hakuri ya je Gusai yaga innani, itama duk ta damu fadi take"Ka gaisheta Assadiq. Allah ya tashi Kafad'un Innani." Ya rika amsawa da Ameen Hankalinsa ya tashi da wayonsa bai san Lokacin da innani ta kwanta asibiti ba, ko ciwo ta ke yi ta gwammace ta yi ta shan jike jike. Yaje ya iske innani an dawo ma da ita gida, bayanta ne wato kugunta ya Bugu, zai zazzabi a jikinta likitoci sun ce a daina barinta ita kad'ai Tunda jikinta na Tsufa ne ta na Bukatar wani mataimaki. Sai ga Innani kwance shuru baki ba mgana, sai ido kawai ta Saduda ta ga mutuwa. Sadiq shi ya yi ma Abba mganar ko cikin ya'yan Su goggo Husai ya Dauko daya daga cikin su ta dawo nan da zama a sakata makaranta. Wacce zata rika kwana da Innani ta na kula da ita. Shawaran Magajin gida ita tayi aiki, Mutanen Shinkafin daman sun zo Dubata, Da Abba ya yi mganar da Dan'uwansa  sai yace akwai Autar Hussai, Farida ta na jss2 ne yasan zata iya kula da Innani. Haka ko akayi ana mgana Hussai tace ta ba su Farida har abada, Kwana daya Tsakani ta had'o kayanta ta dawo Gusai da zama. Cikin Sati daya aka sama mata Gurbin karatu a makarantar da su Sultana ke zuwa,kuma tare a ke kaisu Direba kuma ya Daukosu. Sultana ita gidanta ta ke tafiya ita da Siyama mai tayata zama, ita kuma Farida ta na shashen Innani. Gata ba ta da kiyuwa, ga son aiki da kazar kazar Umma da Abba sun yaba da ita sosai. Innani duk masifarta sai da ta ragama Farida ganin yadda ta ke hidima da ita, sai dai suna tafka tsiya in Tace zata yi ma Innani Jagora ko zuwa daki ko makewayi. Sai Innani ta fara fad'an ita ba makaunniya bace kada Farida ta raina mata wayau mana. Ita ko sai tace to in ke ba mahaukaniya bace ki cire gilashin mana kuma ki yi tafiya ba sanda mu gani. Da Innani taji haka sai bakinta ya Mutu, tasan Faridan na taimakonta kuma duk inda Mutum ya ke Rahama ne, ta na jin dadin jin motsinta kusa da ita ballatana da tare suke kwana su tashi, bakin Innani ya Bude hira chau cau, labaran tsoffin garin shinkafi ba wanda Innani ba ta bata ba, har da Labarin kakarta da irin kishin da ta yi da Innani, yo ina ruwan Innani watarana ma cikin zencen har Hussai din ta ke zagewa in yan tsiyanta suna wajen An dai samu ta Rage tsine tsine ammh fa watarana in aka tabota yini zatayi Allah ya tsine ma uwar barawo tun ballatana in ta ajiye abu bata gani ba, wani Lokacin kuma manta inda ta ijiye take yi sai ta fara jan Hanci ta na Tsine ma barawon da bata gani ba da Danginsa gabadaya. *Janafty* *TMWBK3003* *TMW is a paid Novel, Pay 500 for regular or VIP N1K, Via 0552179550 Jamila Umar Gt bank, 09069067488* https://chat.whatsapp.com/IhAz8h8nRy250ZnGGXwM65 Mai_Dambu Candy world's and more. Zaa iya samun Tuwon madara da iloka, gullisuwa, aya mai sugar, gyada mai gishiri, sannan muna bada sari, muna kuma karban oda da aikin biki ko suna. Muna karban aikin donut da cincin..08130269641 *Bayan Wattani Uku.* Wattani ukun da suka shud'e na yi su ne cikin farinciki tare da tsananin kulawa ta bangaren Assadiq da yan'uwana, Tunda a yanzu cikina na cikin wattani na shida da kwanaki ne har na fara Awo a asibitin musulmi. duk da Assadiq yaso na sauya asibiti, ni nace ya barni anan saboda Cousin din Safiya Sister Zainab, mun saba da ita sannan ta na kula dani, tare da bani shawarwarin da suka kamata. A yanzu haka mun samu Hutun First Semister ina gida in da Allah ya taimakeni kenan, saboda Cikina ya yi wani irin girma na ban mamaki kamar ya na cikin wata na tara. Ban yi kiba ba, sai dai na Kumbura kafafuwana da hannayena tare da Fuskata, komai ada da ya ke karami yanzu ya koma Babba. Na zama wata katuwa sai Ciki mai Tsini ta gaba, ga uban nauyin da cikina ya ke yi, ina jinsa har a jikina Da Kafafuwana kuma har a asibitin na yi Korafi suka tabbatar min da komai lafiya namiji suka gani shiyasa na ke jin nauyin cikin a jikina. Tuni na daina Amai, sai dai na kan yi in naci wani abun da cikina ya kasa karb'a Miyau kuma na daina ammh wani Lokacin sai na kasa had'iyam miyau sai na Tofar da shi. Zazzabin dare shima ya tafi, sai kananun cuwuka da ba'a rasa ma su Ciki da shi. A baya na dauka cewa iya son da na ke yi ma Assadiq ya isa ya rikeni ni da shi a zaman auren mu, Sai daga baya na Fahimci nima ina bukatar Soyayyarsa, Kuma sai a lokacin na kara tabbatar ma da kaina Assadiq ya na sona kuma zai iya komai Saboda ni. Kuma ya na son cikin jikina ya na kuma Burin samun Tsatsso daga bangarena. Gatan duniya da Miji ke yi ma matarsa Assadiq na yi mini shi, Har fiye da zato na da Tsammanina, Ko da yaushe cikin kira na ya ke yi yaji Lafiyata, in kuma ya samu sarari ko ba ranar zuwansa Zariya ba ne zai samu lokaci ya zo ya ganni ko da bazai kwana ba. Bai taba bari na yi kukan wani abu ba, Duk abunda na ke so kafin nayi mgana ya riga ya yi min shi. Kayan abinci wani baya karewa ya ke tarar da wani, komai na Bukatar macen kwarai a gidan mijinta Allah ya bani shi ta bangaran Assadiq ta ko'ina Rayuwata ta inganta. Kudi bani da matsalansu har ma ina taimaka ma yan'uwana, Amma ma dagachan bangaran ina taimakon su da iya abunda na ke da shi. Sun zo kwanaki ita da Adda suka Dubani ba su dai kwana ba ne, Amma daman bazata iya kwana a wajena ba, da ma dai gidan Adda Fati ne, gidan Adda Rukayya daman Saboda Mijinta ba ta cika ganin baki ba. Bangaren Maman Suhailat itama Tsakaninmu sai godiya sosai ta ke kula dani, in dai ta na gida sau ukun nan zata lekoni taga lafiyata shiyasa da Assadiq ya yi mganar kayan Haihuwa da nawa nace ita zan bamawa ta Siyomin ta na da kirki. Nasan yadda zaman gidan haya ya ke, ana samun mutanen kirki da na banza ita dai maman Suhailat ko da ta na da wani halin to kirkinta duk ya shafe wannan. Ramatu da tazo ta ga irin gatan da na ke ciki sai da ta kara dawomin da mganar da ta tab'amin shekarun baya. Ta kalleni da tsinin Cikina a gaba kafin ta yi mirmishi tace"Kawata daman ai na fad'a miki watarana Zaki ji dadin Rayuwa kamar kowa koma fiye da kowa." Na kalleta cikin mirmishi kafin nace"Hakane wlh gashi komai ya wuce sai dai Tunawa." Ramatu tace"Kin tuna na sha gayamiki Daga salisu har Abubakar ba su ne gwanayen ba  gwanin in  yazo Shine yardaddaje har a wajen Ubangiji ki ka yi ta min musu kina ganin kamar haka bazata faru ba, yau gashi kin samu fiye da zaton da na yi miki Fata Hasiya." Sai na kasa yi mata mgana ina ta shafa Cikina ina jin wani farincikin zamowa uwa a cikin raina. Yau ga shi ni Hasiya da na cire rai ga aure ma, ni ce dauke da cikin Haihuwa lalle Allah ne abun godiya Rayuwata daidai ta ke tafiya sai dai abu d'aya ne na ke tunawa ya sakani Fargaba  shine na rashin sanin gobena a cikin Ahalin Assadiq tunda har yau ba su san da zamana ba. Ramatu ce te katsemin Tunani da cewa"Ke na manta ban fad'a miki ba, ranar na shiga anguwan su Salisu na had'u da shi" Cikin mamaki na dago ina kallonta kafin nace"Haba? Me ki ka je yi? Ramatu tace"Makociyata din nan, Maman Basma mahaifiyarta ta rasu naje mata gaisuwa sai naga ashe kusa ne da gidan iyayen Salisu, aiko ina fitowa sai ga shi mun had'e da shi, shi da Musabahu." Cikin wani yanayi nace"Allah Sarki? Ya kika gansa? Ya warke? Ramatu tace"Ya warke, sai dai har yanzu ya na dan d'ingishi, sannan ya na Dogara karamar sanda." Sai na yi shuru na kasa mgana acikin raina ina jin wani iri, kenan har gobe in aka kalli Salisu Bakin Fentin da na yi ma Rayuwarsa bazai taba goge masa ba. Kila Ramatu ta Lura da sauyin yanayina ne, kuma tasan saboda mganar ne, yasa da sauri ta dafani ta na fad'in"Kinga ba na gayamiki ba ne saboda ki shiga damuwa ba, na fada miki ne saboda sai da ya tambayeni ke, yace yaji an ce kin yi aure nace masa Eh! Sai yace in mun had'u nace ya na gaisheki" Kai kawai na kad'a kafin nace"Ayya Ramatu ina amsawa! Ammh dai ko da ya warke, akwai wannan tabon a jikinsa in shi bai kirani bakar Daka ba, yan'uwansa baza su taba mantawa dani ba." Ramatu cikin wani yanayi tace"To ai ba ke bace Allah, ke dai kawai kin zama Sanadi ne Hasiya, ki kara godema Allah domin kin cinye jarabawarki." Sai kawai na gyad'a kai kafin nace"Hakane ina Labarin Abubakar? Ya dawo garin ko ya na chan kanon? Ramatu tace"Anya? Kinsan bansan kowa daga bangaransa ba, ko ya dawo kila dai ya na chan, ko kilama ya yi auransa." Da Sauri nace"Allah yasa." Daga haka muka saki maganarsu muka kama wata, sai dai har ta tafi abun na cikin raina. Yanzu Fargabata d'aya yan'uwan Assadiq ta yadda zasu karbi' mganar auranmu daga sama, ni abun da ke damuna in suka ji Bakin fentin da ya bata Rayuwata dakyar su amince Assadiq ya cigaba da zama da ni. Ga cikinsa a jikina in har ya barni bansan kuma wani Hali zan shiga ba. Da farko farko na dauka in ma yace baya son cikin ni kad'ai zan iya renen Cikin har na haifesshi na bashi Soyayya da kulawa, sai daga baya na Fahimci wani abu ni kad'ai bazan iya ba. Assadiq shi ne ginshikina ni kuma ni ce mahad'in Rayuwarsa da Rayuwar abunda ke cikina gabadaya. Ko da yaushe cikin Tuna ma Assadiq na ke yi akan ya yi ma yan'uwansa maganata su san da ni, ammh sai yace na kara masa Lokaci in sha Allahu zai sanar da su, abunda na lura shine tsoro ya ke ji, kuma ya rasa ta hanyar da zai iya fad'a musu kuma Lokaci na ta tafiya, Tsoro na d'aya in har na Haihu wlh abubuwan za su kwabe mana yadda bamu yi tsammani ba. Kuma in har na Haihu nasan yan'uwana za su bukaci ganin Dangin Assadiq rashin ganinsu zai iya fassara karyan da na yi musu. Ammh bayan wannan fargaban babu abunda ya tab'a Rayuwar auran mu, cikin Farinciki mu ke zaune tare da Soyayya da kauna da Tunanin Dorewa na har Abada. In ya zo min weekend kashe wayoyinsa ya ke yi, sai zai kira Sultana ko gida sai ya kunna ya yi mgana da su, Lokacinsa da komai nawa ne, ba na girki sai dai ya Daukeni a mota mu fita mu ci a waje, mu ne wajen shan Ice cream mu ne wajen cin abincin da cin kayan kwalama, ba kowani zuwa ya ke zuwa da mota ba, wani Lokacin sai ya biyo ta haya. Ya sauyamin waya ya siya Wata Samsumg Sabuwa, sannan ya siyamin wata karamar Tap mai kyau, har sai da na yi masa mgana baya gajiya da siyan computer, ko wani Lokaci sai na gansa da sabuwa ? Sai ya yi dariya kafin yace min sana'ar Abba kenan ya na shigo da su daga china, india zuwa Gida nan Nageria. Daganan na yi shuru Tunda abun na masu uwa a gidin Murhu ne, Karamin Tap din sai na ke zuwa makaranta da ita babba kuma sai na rika barinta a gida na kallo na ko yin game da Sauran abubuwa. Saboda gudun a samu matsala ko Hotona ba na Dorawa a waya Tunda Saliha na da lambata, sai dai in muka yi Hotuna na adana su a wayata, shima baya Turawa saboda gudun a samu matsala  sai dai ya kan dauki wayata mu yi ta Hotuna da shi. Akwai wani zuwan da ya yi lokacin cikina ya shiga watansa bakwai kenan ya kara girma da tsini. Zamu fita ne zuwa gidan Ramatu daganan mu je gidan Adda Fati, na saka bakar Abaya na yi Rolling din mayafin shi ya ma nad'amin shi, shi kuma ya sanya Farar shadda har da Hula sai ya zama wani babban mutum kwarjinsa ya kara bayyana. Rikeni ya yi ta gefen Damarsa ni kuma sai na kwantar da kaina saman kirjinsa, shi ya Dauki wayata ya yi mana Hoton ni na dago ina kallon wayar shi kuma ya na kallona dukkanmu muna Dariya aka yi Hoton Farar Fuskata da ta kara wani haske ta bayyana acikin hoton shima Saboda Hutu ya kara fari da kiba sai muka yi wani irin kyau kamar Wasu Taurari acikin Wata. A mota ma ni na kara yi mana wasu Hotunan ya na Tuki ina faman Sauke kaina saman kafad'ansa ina yi mana Hotuna har da Vedio. Mun yi kyau sosai shima da muka Dawo gida na nuna masa yace Hotunan  sun yi kyau na ijiye mana watarana zai saka a wanke mana Babban Frem dinsa. Abunda bansani ba Shine ni dai nasan ba wanda ke Daukan wayana shiyasa ban taba Tunanin Samar ma Hotunanmu muhallin sirri ba, na manta Safiya na Daukan wayata, a satin da muka yi Hoton muka koma makaranta a chan ne Safiya ta karb'i wayata ta na gani sai ta ga Hotunan nan Sai ta fara santin mun yi kyau, Daman kuma tasan Assadiq tunda sun taba had'uwa yafi sau biyu. Bayan Hotunan mu ina da littafan Hausa a wayata, wanda na kan samu a groups din novels, su ne su ke debemin kewa in Assadiq baya nan, duk da karatun ba sosai na ke yi ba su Safiya tace min zata Tura bansani ba ashe ta had'a da wad'anan Hotunan ta Tura cikin wayarta. Wad'anan Hotunan su ne za su sillar fallasa Sirrin da Assadiq ya jima ya na Boyewa. ******** Saddiqa da ke aure a Jahar Kebbi yar kasuwa ce sosai, ta na kasuwanci saida atamfofi lesuka da Sauransu, sannan a cikin Family ko biki za'a yi ita kan fito da anko kuma ta Dauko. Shiyasa ta na harka da yan kasuwa yan'uwanta daga mabambanta garuruwa. Kuma harkan ta yafi yawa ne ta Kafafen sada zumunta, ta na da mutane sosai ma su kallon Status dinta, da kuma wad'anda ta ke huld'a da su. Da safiyar ranar wata Laraba bayan ta gama abunda ta ke yi ta sallami yara da megidan ta dauki wayarta, akwai kayan data siya daga kano ta siya kayan za'a tura jigawa, ta na so ta yi mgana da mai shagon taji in har an gama had'a kayan gabadaya. Ta na Bude data sakonni suka yi ta Tururuwan shigowa, Sai da ta bari suka gama shigowa sannan sai taga ma agent din yaron shagon ma ya yi mata mgana sai ta Bude ta na gani. Vioce ta yi masa bayan ta ga hoton kayan da daukan mata, akwai sauran kudin da zata tura musu, sai da ta gama duba komai taga sun yi, sannan ta sauka ta tura musu Ragowan kudin, ta dauki Trancsation din ta Tura masa tare da lambar wacce za'a aika ma kayan Tunda su za su ba da akai tasha a saka a motar jigawa. Ta na ganin ta gama da wannan bangaran, sai ta fara duba Sakonin mutane ta na ba su amsa bata ma gama ba, ta tafi kallon Status din Sauran mutanenta. Har ta wuce Status din Khairiya Ahmad, sai ta dawo saboda ta na saida y'an kunnaye ma su kyau ta na so ta siyan ma yara, sai ta shiga ta fara Dubawa, ta santa tunda suna harkan kasuwanci tare ba su dai tab'a ganin juna ido da ido ba sai a hoto. Ta dai san kamar Khairiya ta tab'a Fad'a mata ita yar zariya ce. Kamar wasa ta na gama ganin Hotunan y'an kunnen sai tayi Tagging din na karshen ta yi mgana. "Salam Khairiya wannan akwai na yara irin shi? Sai kuma ta kara da cewa"Au bamu gaisa ba ina kwana ya kasuwa? Sai ta fita ganin kamar ta na Online ammh kuma kamar ba ta kusa da wayar. Ijiye wayar ta yi itama ta je kitchen domin ta saka ruwan zafi ta na dafa Indomie ne, yau yaran da megidan Plantai suka ci da Tea ita kuma ba ta cika son plantain ba. Sai da ta gama Dahuwarta ta dafa kwai sannan ta Zubo a filet ta fito da shi falo ta ijiye saman Center table din da ke falon. Wayarta ta dauka sannan ta fara cin abinci, ta na ci ta na duba wayarta, Khairiya ba ta duba sakonta ba sai tayi tunanin kila har yanzu ba ta zo kusa da wayar ba. Sai ta koma Bangaran Status sai kuma taga sunan khairiya alamun ta kara saka wani Status  har ta wuceta sai kuma ta dawo ganin kamar Hoto taga ta saka, sai ta dawo ta Bud'e. Abunda ta gani ne yasa sai da  cokalin hannunta ya subuce ya fad'i kasa. Da sauri ta mike jikinta na rawa har ta barin Ruwan da ke karamin kofin Tangaran a gefenta. Cikin Firgici da rawan baki tace "SADIQ." Hannunta na rawa ta kara Zooming din Hoton domin ta kara tabbatar ma da Idanuwanta shin abunda ta gani gaskiya ne? Sadiq ne ta ke gani tare da wata mace da ciki, sannan a yanayin Hoton cikin Halin da mata miji ko farka kan kasance ne a ciki. Saboda Tsabar Rud'ewa ta manta da Duba abunda Khairiya ta saka a kasan Hoton sai da ta dauki Hoton ta koma kan wayarta ta kara Duba shi da kyau. Tabbas wannan Sadiq ne to Sadiq din ne bata sani ba Allah na Tuba ko cikin Duba sai ta iya Cire kanin na su. Zama ta koma ta yi Saboda jin wani jiri na Dibanta. Da Rawam jiki ta kara komawa ta Duba Status din khairiya sai alokacin taga abunda ta saka a kasan Hoton. "Jama'a See Love don Allah? Mu ma Allah ya aurar da mu" Tare da saka Emojin kunya da Love. Saddiqa sai ta kasa ma wani Tunani, kada ta ce ba ta da tabbacin ba Sadiq ta gani ba domin shi ne ta gani a wannan Hoton tare da wata? To in shi ne ta jikin Hoton wacece? Sai ta kasa ba ma kanta amsa lokacin da wani shashe na zuciyarsa yace"Karuwar sa mana." Tunda dai mace daya garesa itace Sultana to in dai ba Sultana bace wacece? Kuma a yanayin da suke a tare tabbas in ba mata da miji ba to su farkan juna ne. Hankali tashe Saddiqa ta lalubo lambar Surayya ta doka mata kira ammh har ta gama ringing bata dauka ba, Sai zuba Zufa ta ke yi lokaci d'aya ta na fad'in"Ki daga mana, ki daga mana Big sis." Ta ke fad'a ta na faman zagayen falon cikin tashin Hankali. Kiran da ta yi ma surayya yafi goma ammh bata daga ba, sai ta yi tunanin Tabbas bata kusa da wayar. Ta rasa wa zata kira, Surayya ce babba kuma kafin umma taji wasu matsalansu ita ke fara ji, kuma ta tayasu warware shi cikin sauki. Ta yi Tunanin ko kiran Sa'ima ammh kuma sai ta fasa, in kuma ba shi ba ne fa? In har maganar ta fita Sun zubar ma kaninsu kima da Darajarshi da sauran suke gani. Rashin Daukan wayan Surayya yasa ta kara komawa ta na ta duba Hotunan nan, ta na kara Zooming tuni idanuwanta har sun ciko da kwallah, sai a lokacin ma taga kamar tasan yarinyar jikin Hoton ammh ta rasa inda ta santa. Sake komawa Chart din ta yi sai taga Khairiya ta sauka daga online da gaggawa ta kirata, kuma ba sa ma kiran juna in ba kasuwanci siyan wani abu ya had'a su ba. Itama sai da wayar ta kusa katsewa sannan ta dauka. Bayan sun gaisa Saddiqa tace"Khair na yi miki mgana ta chart baki Duba ba." Dagachan Bangaren khairiya tace"Sorry na ijiye wayar ne muna mgana da Mama? Lafiya ko wani abu ki ke so ne? Saddiqa tace"Eh na yi miki mganar wasu y'an kunne ne ko akwai na yaran su? Khairiya tace"Ok in na duba zan miki mgana, Nagode" Har khairiya zata sauke Wayar Saddiqa tace"Amh Khairiya ni ko nace ba, hoton da naga kin saka dazu amaren sun yi kyau, sai naga kamar kuna kama ko kanwarki ce? Mijinta ne? Khairiya tace"Wacce? Wai HASIYA? ba kanwata ba ce kawar kanwata ce Safiya a wayarta nima naga Hoton sun yi min kyau sai na Tura shi a wayata shine har na yi status da shi Eh mijinta ne." Saddiqa cikin mamaki tace"Allah sarki! A nan zariyan su ke kenan? Khairiya tace"Eh anan zariya su ke" Saddiqa sai ta rasa kuma abunda zata ce, kiran wayarta taji ana yi, ta na Dubawa sai taga Surayya ce kiranta da Sauri ta yi ma khairiya sallama. Ta daga kiran Kiran Surayya. Wacce ta na dagawa tace"Ke lafiya naga uban kira Rututu? Saddiqa ta sauke Numfashi kafin tace"Big sis ki zo online zan tura miki wani abu yanzu nan." Dagachan Bangaran Surayya tace"Miye? Lafiya ki ke kuwa? naji muryanki ta yi kasa ne." Saddiqa tace"Big sis ki je ki ga abunda ya sakani firgici don Allah" Jin haka yasa Surayya tace shikenan Hankalinta ya tashi ganin kiran Saddiqan ba adadi. Da sauri ta Bude data, Daman dazu wayar na daki ne ita kuma suna falo megidanta na karyawa sai da ya gama ta rakasa ya fita aiki shine da ta dawo dakin taga kiran Saddiqa ba adadi. Ta na bude data ba ta tsaya sauraran kowa ba sai sakon Saddiqa da ta jira ya shigo ta na shiga sai taga Hoto ne. A kasan Hoton Saddiqa tace"Don Allah Big sis wa ki ka gani cikin Hoton ga? Sai da ta Bude hoton, irin razanar da Saddiqa ta yi, Surayya ta fita shiga tashin Hankali domin sai da wayar ta subuce daga hannunta ta fad'i saman Cafet Saboda gigita da Dimauta. Sai da ta kara Dauko wayar ta sake bin Hotin da kallo, ai ba ta bukatar ta yi zooming ko mutuwa ta yi ta dawo zata iya shaida kaninta a cikin Dubban Mutane. Wannan ai Sadiq ne! Sadiq shinkafi ne kaninsu to shi da waye? Ita yarinyar ta rika kallo ma, sai ta ke ganin kamar tasan fuskarta cikin jikin yarinyar shi yafi komai jan Hankalinta Saddiqa na ta turo mata mgana ba ta Dubawa. "Big sis Sadiq ko? Ko ba shi ba ne? "In da naga Hoton, tace wai mata da miji ne? Sadiq na da wata mata ne bayan Sultana? "Kin yi shuru? '"ni macen Hoton ne na ke ganin kamar na santa." Sakon Saddiqa na karshe yasa Surayya ta kara Duba Hoton macen da kyau, Tabbas tasan wannan Fuskar, kuma kamar a gidansu ta taba ganinta, zama ta yi ta na kallon Hoton ta na so ta tuna inda ta taba ganinta Momorig lokacin na Shiga kanta. Kamar an Tuna mata sai taji ta tuna a da inda ta tab'a ganinta kawar Saliha da ta zo bikin Sultana. Da Sauri ta kira Saliha tace ta Hau chart zata Tura mata wani Hoto. Gudun abunda zai je ya dawo sai ta yanke Hoton Sadiq ta Tura mata na Hasiya sai da ta tabbatar ta gani sannan ta  kara kiranta Ta na Dauka Surayya tace"Saliha kamar kawar nan ta ki ko? Saliha tace"Kwarai HASIYA ce. Ba ta zo min bikin Sadiq ba? Kin manta wacce na ce muku a kaduna muka had'u yar'uwan mijin Salima ce fa." Surayya sai jinjina kai ta ke yi cikin Tsananin mamaki kafin tace"Na tuna ta wata tfara haka  har ma kika bani wayarki na yi muku Hoto ko? Saliha tace"Kwarai ashe baki manta ba, bari na tura miki hoton ki kara gani, anan ta yi kiban fuska ne kila Saboda cikin jikinta ne, ni ban ma san ta na da ciki ba, kwanaki dai da muka yi waya tace min ta yi ta fama da Zazzabi." Surayya sai ta kasa mgana ji ta yi zufa na keto mata ta saman goshinta, duk da AC Din da ke falon. Cikin wani yanayi Surayya tace"Da bikin sun had'u da Sadiq ne? Saliha ta yi shuru kafin tace"Gaskiya bazan iya tunawa ba? Hala me ya faru? Da Surayya tace"A'a bakomai, wata kawatace naga ta  saka a status sai na ke tunanin inda na taba ganinta." Da haka ta shanshantar da mganar Saboda kada Saliha ta fahimci wani abu. Sai gashi kafin ma ta tambayeta Saliha ta fara gayamata Hasiya ta ja baya da ita, ba kamar farkon fara kawancen su ba. Surayya ta koma ta zauna Dafe da kai bayan sun gama mgana da Saliha a waya. Jikinta gabadaya ya saki bata so ma ta yi wani Tunani sai kawai ta fara maimaita"Innalillahi wa'inna ilaihirraju'un" a cikin zuciyarta. Wacece wannan yarinyar Tare da Sadiq? Me ye alaqarsu da za su yi Hoto rike da juna haka? A ina zata samu amsar Tambayoyinta? Kiran Saddiqa ya katse mata Tunani da Sauri ta daga kiran ta na fadin"Saddiqa Sadiq ne a wannan Hoton." Saddiqa tace"Innalillahi Sadiq ne? Surayya tace"Ba tabbaci gareni ba, yakini ne da cewa shi ne Saddiqa" Saddiqa ta share zufa kafin tace"To in dai shine to miye alakarsa da wannan yarinyar? Surayya tace"Sunanta Hasiya, kuma yar'uwar mijin Salima ce, itace kawar da Saliha ta yi a kaduna, ta kuma zo bikin su Sultana Shiyasa ki ke Tunanin kin santa" Saddiqa ta saki baki kafin tace"Tabbas an yi haka sai da kika fad'a na gane? Wacce Saliha tace ta tafi ba ta yi mata sallama ba? Surayya tace"Saddiqa ki bar mganar nan a tsakanin ni da ke, zan yi yadda zan yi na binciko komai  ammh kema ta bangaranki ina so ki samo min address din in da yarinyar ke zaune." Saddiqa tace"Big sis Khairiya tace min fa matar aure ce kuma a yadda abun ya ke, Sadiq shine mijinta wai" Surayya tace"Duk da haka muna so mu san inda ta ke, ki kace a zariya ko? Saddiqa tace"Eh haka tace" Kawai sai Surayya ta yi wani Dariya takaici kafin tace"No wonder" Daga haka ta katse wayarta, ta fara safa da marwa a tsakar falonta. Ta na sake maimaita sunan Hasiya da Zariya. Sai kawai ta fara Tunano yadda Sadiq ya nace ma karatu a zariya, ya gama yace bautar kasa, ya gama yace aiki zai yi achan sai ya fake da karatu, ta tuna ya na yawan ambaton wata ASIYA da sunan abokiyar aikinsa, kenan in ta hasaso daidai su Sadiq ya maida kananun yara ya ke wasa da Hankalinsu? Koma wacece wannan yarinyar akwai alaqar da ta yi karfi a tsakaninsu wacce ba su sani ba, ita ko kadan bata bari Tunaninta ya bata wani mugun abu Sadiq ya ke yi ba, Tunanin ya fi karkarta kan abunda Sauran ba su hasaso ba. Wayarta ta sake Dauka da Sauri ta Kira Salima ta na tambayanta ko ta na ina? Sai tace mata ta na makaranta. Kai Tsaye Surayya tace"Salima me kika sani kan wannan yar'uwan mijin naki kawar Saliha? Salima tace"Wacce Big sis? Ban ganeta ba? Surayya tace"Wacce suka had"u lokacin bikin ki, ta kuma zo bikin su sultana.". Salima da ke tare da Zahra'u a makaranta domin ta fara karatu a kasu, kaduna State University. Tace"Oh na tuna me ya faru da ita? Surayya tace"Kinsan ta sosai ne? Salima tace"a'a ni ban kara ganinta ba, hala me ya faru? Surayya tace"Taimako na zaki yi, ina son sanin labarinta ne, ko shi Mubark din ki tambayeshi mana." Salima tace"Ok! Sai Surayya tace zata Tura mata Hoton ta, Tunda ta lura kamar Saliman ba ta maida kai kan mganar da ta ke yi mata ba. Da Sauri ta Bude data sai ga Hotunan Saliha ta Turo mata harda wanda ta yi mata ita kad'ai Tabbas wannan yarinyar ce. Da Sauri ta Dauka ta Turama Salima, ta kuma kara kiranta tace ta bincika mata da Sauri don Allah. Jin haka yasa Salima cikin Tunanin to lafiya? Ta dai san me ya had'a Big sis da neman Labarin wata!? Sai dai sanin kawar Anty Saliha ce sai bata damu ba nan ta ke ta Bude datan ta, ta shiga ta ga Hoton da Big sis ta Turamata sai a lokacin ta kara gane Matar da ake mgana a kanta. Zahra'u ce ta leka ta na ganin Hoton sai taga Hasiya da Sauri tace"Hala wannan ai Hasiya ce" Salima sai ta kalleta kafin tace"Eh itace kinsan ta ne sosai? Sai zahra'u ta girgiza kai kafin tace"Gasiiya ba sosai ba, ni ma da Bikin ku ne na santa, da ya ke Baba bai cika barin mu, muna zuwa zariya ba, sai dai su zo" Sai salima tace"To ki tambayan min ko Baba ne kin ji ko? Sai Zahra'u tace to shikenan zata tambayan mata, ammh sai da tambayeta me yasa ta ke son sanin Labarin Hasiya? Sai tace kawar yayarta ne ita ke son karin sani akanta. Sai zahra'un ta gamsu da maganar Salimar kamar yadda, itama Salima ta gamsu da cewa dalilin da ya sa Big sis din ke son ta sani kenan. Ita kuma ta bangaren Surayya, sai da ta gama Tunaninta gabadaya sannan ta daga waya ta kira Sajida tace anjuma tazo gidanta ta na nemanta. Sajida kuma daman uwar son jin mgana ne da zence, ba jimawa sai ga ta tazo, itama Hoton Surayya ta nuna mata tace ko ta gane waye? Da sauri ta Mike ta na kwalalo ido Lokaci daya ta na fadin"Mun shiga uku, kamar Sadiq? Surayya tace"ai ba kama bace shine." Sajida ta dafe kirji da karfi kafin tace"Shi ne? To ita wannan macen da ke tare da shi fa! Wacece? Surayya tace"Shi na ke son sani yanzu, ki kara kallonta dakyau zaki ganeta, kin taba ganinta kawar Saliha da ta zo bikin sultana wacce tace yar'uwan mijin salima ce." Sajida sai ta kara zooming din Hoton ta na gani kafin tace"Tabbas ba musu itace, kinsan ai fara ce sosai shiyasa na ga neta. Big sis sadiq me zai ja mana? Ba dai ya koma Bin matan aure ba ne? Ta fad'a cikin tashin Hankali, Surayya ta Girgiza mata kai kafin tace"Ba na wannan Tunanin Sajida, a sanin da na yi ma Sadiq mutum ne mai ilimi da sanin ya kamata, ba zai aikata haka ba." Sajida ta koma ta zauna da yarta a hannu lokaci d'aya ta na fad'in"Big sis kaina ya Daure? Ko da bikin ne suka had'u da juna? Surayya na kallon wani gefe tace"Ba'a lokacin ba ne, sun jima da sanin juna Sajida." Sajida ta yi shuru kafin tace"Big sis wlh na shiga Rud'u, me ke shirin Faruwa ne? Surayya ta koma ta zauna gefen Sajida Ta na fadin"Koma wacece to alaqar da ke tsakaninsu ba ta haramci ba ne." Sajida tace"To alaqar uwar menene tunda ba aure suka yi ba? Surayya ta kalleta kafin tace"In kuma ace sun yi auren fa? In kuma ace ita din MATARSA CE.!" SAi Sajida ta zabura kafin tace"Matarsa? Cikin Dimuwa, surayya ba ta sami zarafin magana ba, kiran Saddiqa ya shigo wayarta da Sauri ta Daga. Mirmishi kawai ta ke yi na dacin zuciya da takaici, Saddiqa na gayamata ta tura mata adireshin inda Hasiya ke zaune, kuma har da karin Shedar mijinta ma'aikaci ne a garin Abuja. Surayya ta yi ajiyar zuciya kafin tace"Saddiqa mu bar mganar nan a tsakanin mu uku, bayan mu kada najita a waje, ni da Sajida gobe in sha Allahu zamu tafi zariya domin mu kara Tabbatar da zargin mu." Saddiqa tace"Gaskiya ya kamata, ni wlh duk na Rude, Umma kawai na ke tunawa, fata na Allah yasa ba Sadiq din mu ba ne" Surayya bata ce komai ba ta katse wayar, a ranta ta na tunanin suna ma yaudaran kansu ne in suka ce wai ba Sadiq din su ba ne. Sadiq ne shine ajikin wannan Hoton ba wani ba. Sajida ta katse mata Tunani da fadin"Me zamu je yi a zariya? Surayya ta mike ta na fadin"Sanin gaskiya, da kuma sanin abunda ke Boye game da Rayuwar kanin mu da bamu sani ba Sajida." Sajida sai ta kasa mgana itama har taji idanuwanta ya kawo kwallah. Me sadiq ya ke aikatawa ne a wannan garin? Daman shiyasa ya nace ma garin, har Sa'insa ya fara yi da su saboda haka ashe ashe. Allah yasa ba abunda suke zargi ba ne Allah ma yasa kama ce ba shi ba ne. Surraya tace bayan su uku kada wani yaji wannan mganar sai ta gama Bincikan gaskiyan Lamarin Sannan tace ko Sadiq kada su bari ya Fahimci wani abu. Za su je zariya kuma zasu tono abunda Sadiq ya dad'e ya na Boye musu. Daman kuma ta Fahimci hakan Tuntuni, rashin Hujja ce yasa ba ta taba Furtama kowa ba. Sun Rabu da Sajida akan sai goben, Direban mijin Surayya zai tukasu zuwa zariya, ita kuma Saddiqa daga bangaranta surayya tace ta jira su Dawo daga zariyan Saddiq ita kanta hankalinta a tashe ya ke, Wayau ta yi ma Khairiya tace ashe Hasiya kawar wata kanwarta ce, sai daga baya ta ganeta, daman kuma ta rasa lambarta ta na son adireshin Hasiya saboda kanwar nata na son in ta shiga zariya taje wajen Hasiya. Shine khairiyan tace bari ta yi ma kanwar nata mgana, sai gashi har da lambar Hasiyan aka Turo mata. Daga khairiya har Safiya ba su san abunda hakan zai haifar ba. Ballatana Hasiya da ke chan bata san abunda ke faruwa ba. Uwa uba Uban gayya Sadiq da ke chan Abuja kan aikinsa bai taba kawo ma kansa abubuwa zasu lalace masa batare da ya sani ba. *Janafty* *TMWBK3004* *TMW is a paid Novel, Pay 500 for regular or VIP N1K, Via 0552179550 Jamila Umar Gt bank, 09069067488* https://chat.whatsapp.com/IhAz8h8nRy250ZnGGXwM65 *LAME NIG!* *KASAITATTUN MATA MUN GAISHE KU*. *AISHA LAME TA KAWO MUKU DUKKAN NAU'IN KAYAN KWALLIYA*. *KUNSAN GWANAACE WAJEN BAWA FATA HAKKIN TA* *KUN TUNA KYUAN FATAR GUDUYO KO?* *KUN TUNA DAI YADDA BULKACHUWA KE SIYAWA YABI KAYAN KWALLIYA NA ORIFLAME KO?* *TO KEMA GARZAYO KI ZABI NA KI, KO TA ZABA MIKI WANDA ZAI FI DACEWA DA FATARKI*. *BA IYA KAYAN ORIFLAME BA KAD'AI.* *TANA DA PRODUCTS DABAN DABAN MASU KYAU, MASU MASTAKAITAN FARASHI*. *KU TUNTUBE JIKAR DADAR MARINA A WANNAN LAMBAR 07036662633*. *ADO DA KAMSHI NE SIRRIN GAYU* Washegari. Zariya. Yau Alhamis muna da karatu a makaranta, ammh saboda yadda na tashi cikin nauyin jiki yasa na yanke shawaran bazan fita ko'ina ba. Kafafuna ne na lura yau sun kara tasawa, sannan kamar cikin jikina ya sauka a saman kafafuna haka na rika ji, Dakyar na iya tashi na yi shara da goge goge saboda wajen kwana hud'u ban iya taba komai acikin dakin ba. Assadiq ya kirani Tun asuba shi ya ma tasheni sallar asuba, kuma bayan na idar ya sake kirana mun yi mgana, sai da ya tabbatar da lafiyata kalau sannan yace na koma na kwanta na Huta. Ban yarda na fad'a masa yanayin da na ke ji ba, yanzu sai ya d'aga Hankalinsa ya kasa natsuwa, kuma naga lalurorin ma su cikine, shiyasa ban gaya masa ba dama ya tambayeni zan shiga makaranta ne sai na amsa masa da Eh! Har kuma yace zai Turomin kud'i ya na tunani na hannuna sun yi kasa. Ko da na gama gyaran dakin nan, sai da koma na zauna ina ta faman Numfarfashi na tsawon wani Lokaci sannan na tashi na shiga kitchen na Dumama ragowan Tuwon da Maman Suhailat ta zubomin jiya. Tuwon masara miyer karkashi, rabi na ci jiya na rage na safe, ga uban wanke wanke jibge  na fara tunanin ko na kira Adda Fati ne Habiba tazo? Domin har ga Allah zan sha wahala in nace zan tsaya na yi wannan wanke wanke. Sai da na gama cin Tuwon sannan na fara Tunanin wanke kwanukan, abun dai sai a hankali ina yi ina faman Hutawa, kafin na gama baya na ya kage, kafafuwa sun kara nauyi, ko gyara kitchen din ban yi ba, na koma cikin Daki na kwanta da na huta sosai har sai da naji ina jin barci barci. Sai dai ban kwanta ba, ta shi na yi na sake ruwan zafin da na saka a kittle, na shiga wanka na gasa jikina, da na Fito sai na Shafa mai, saboda kaya na duk sun matseni na dai na saka su, iyakata Dogayen Riguna da T.Shirt da riga da zani. Kuma duka sun yi datti, na had'a zan kira Habiba ta zo ta je gidan Adda Fati da shi ta wankemin, Tunda ni dai yanzu ina gabda daina Daukan Laluran kaina. Sai na Bude bangaren da Kayan Assadiq suke cikin Wadrope d'ina na Dauko wata farar T.Shirt dinsa na saka na dauka ma zata yi min yawa Tunda ta na da fad'i ammh sai naga ta shigeni gabadaya, sai na had'a ta da wani zanin Atamfata na saka Hula. Wayata na dauka na yi masa Hoton kaina da Rigar ina Dariya a raina nace in yazo zan nuna masa rigarsa har ta faramin kad'an. Game na fara yi a waya ta, daganan bansan Lokacin da barci ya kwasheni ba, sai da naji kamar daga sama ana ta Bugamin kofa, na mike da sauri wajen saukowa daga kan gado har sai da naji kafafuwana sun sage, kuguna ya amsa sai da na tsaya na yi salati na d'an sarara sannan na fita zuwa falo ina kokarin gyara hulan kaina. Har na isa kofar dakin knooking a ke yi cikin Sanyin murya nace"A na zuwa." In da ace nasan abunda zan gani in na Bude kofar nan, na tabbata ko da kud'i aka had'ani bazan taba Budewa ba. Gwara rashin Budewan akan Bud'ewan, ina jin d'an cikina na Motsi lokaci bayan Lokaci ammh yau da na ga Yan'uwan Assadiq Tsaye a gaban kofar dakina sai da naji kamar abunda ke cikina yafi d'aya, Saboda yadda cikina ya murd'a naji ta ko'ina ana juyi tare da irin naushi kamar dai akwai abunda yafi d'aya acikin cikina. Tsabar kad'uwa yasa sai naji kamar an kafeni a wajen, bakina na rawa tare da kiftawam idanuwana, zuciyata kuma ta na barazanan fitowa waje saboda Tsabar tsoro da Firgici. Yadda na ke kallonsu ido waje haka suma suke kallona, na gane su bayan ganinsu a hoto dukkansu na gansu a bikin Sultana da Assadiq har mun gaisa. Ina rike da Kofar Rud'ewa yasa na ma kasa saki, Sajida ce ta kalleni kamar Idanuwanta zasu fado kasa saboda takaici Cikin gatsali tace"Ke ce Hasiya? Sai kawai na samu kaina da gyad'a mata kai ina jin marata ta Daurewa kamar ace haihuwa zan yi, Sajida zata kara mgana Surayya ta kalleta kafin ta girgiza mata kai alamun tayi shuru, kaina ta dawo da kallo kafin tace"Zamu iya shiga ciki? Ta fad'a kai Tsaye ta na kallona, sai a lokacin na lura da yadda na tare kofar, cikin daga kafa na matsa baya ina fad'in"Eh eh! Ku shishigo sannun ku da zuwa" Bakina tare da bugun zuciyata su ke tafiya, Surayya ce kan gaba Sajida na bayanta Dauke da yarinyarta a saman kafad'anta. Tsabar Rudewa na kasa bin bayansu, Sai da na tsaya dafe da kuguna acikin raina ina maimaita"Innalillahi wa"inna ilaihirraju'un shikenan abunda na ke ta gudu ya zo ya faru, ai shikenan" In da ina da yadda zan yi bazan bi su ciki ba, fita zan yi na nemi mafaka ammh kuma bani da wata mafita, sai dai a chan kasan raina ina Tunanin ko dai Saliha ce ta aiko su? Sai naji kamar mganar ba ta zauna a raina da hakan zai faru ba. Da jan kafa na kariso falon na iske su har sun yi ma kansu matsugguni a daya daga cikin kujerun falon. Surayya wayarta ta ke dannawa ta yi shigar alfarma sannan Fuskarta bata bayyana abunda zuciyarta ke ciki ba  Sajida ko sai faman kalle kalle ta ke yi cikin Raini da wulakanci. Kamar wacce wani abu ke cizo a kafa haka na kasa tsayuwa a gabansa sai na juya da sauri na shiga kitchen jikina na rawa, na dauko musu Ruwan Gora guda biyu kofi na saka cikin wani Farantin silba. Na Kwaso ina rawan kafa da na zuciya na kawo gabansu na sauke sannan na Durkushe ina jin kamar ina cikin wani abu mai zafi saboda yadda Tsoro da firgici suka saka naji kamar ina cikin zazzabi mai zafi. Surayya ta kalleni yadda na zauna duk a takure sai tace"Ayya kinga ta shi ki koma saman kujera" Kaina na kasa ammh na kasa mgana a raina ina fadin ko dai ko dai? Saboda ban ga alamun sun san wani abu ba. Kamar daga sama naji Tace"Hasiya ko? Sai na dago da sauri ina kallonta kafin nace"Eh eh ni ce." Kai Tsaye tace"Nasan kila kin gane mu, in ma baki gane mu ba mu yan'uwan Saliha ce, mun had'u da ke da kika zo mana Biki a gusau." Cikin yaken karfin Hali nace"Eh an yi haka sannun ku da zuwa." Surayya ce kad'ai ta amsa kafin ta kalleni na wani lokaci. Sajida ta kalleta ta na fadin"Big sis mu yi abunda ya kawomu, na kosa mu bar nan.". Surayya bata ce komai ba, sai dai ta mike ta zo ta zauna kusa dani, jikina na rawa naji na sake zaman Dirshan a kasan Tayels, Kallona ta ke yi ni kuma na kasa kallonta kallo d'aya zaka yi min kasan bani da gaskiya. Cikin Kakkausan murya Surayya tace"Hasiya tambayarki na zo yi takanas daga Gusau zuwa garin da ban taba zuwa ba, kuma ina so komai na Tambayeki ki fad'amin gaskiya, in kuma kika yi min karya nan gaba zai zame miki matsala, ita kuma gaskiyarki in kika tsaidata Allah shi ne zai nuna miki aikin gaskiya, ina fatan zaki fad'amin gaskiyan Abunda kika sani" Ina salati a cikin raina, a fili kuma sai na gyad'a mata kai zuciyata na rawa nace"In sha Allahu zan fad'a miki iya gaskiya abunda na sani." Sai ta gyad'a kai kafin naga ta Dauko wayarta ta Danna ta saukemin wayar a saman Fuskata, lokacin da na yi arba da Hotona ni da Assadiq sai da naji na fara fitsarin da na matse, cikin gwalalo ido na kalli Hoton sannan na koma ina kallonta tare da mamakin ina suka samu wannan Hoton?. Ko Assadiq ne ya nuna musu? In kuma ba shi ba ne, na tabbata yau karya ta kare, sannan kuma muna cikin Tsaka mai wuya. Surayya sai da ta gama ganin yanayin Firgicina sannan tace"Waye wannan a tare da ke? Wace alaqa ne a tsakanin ku? Mun ga Hoton a Duniya, mu kuma bamu san ke wacece ba, gudun yanke Tunanin da ba shi ne ba, sai na yi Tunanin na Bincika komai kafin mgana ta kai wajen manya." Ta dakata ta na Sauke Numfashi ganin har na fara sharan hawaye. Cikin kasa da Murya tace"Ni sunana Surayya kuma ni ce babba a gidanmu, ina daukan girman da Allah ya bani da Muhimmanci, Hasiya ki gayamin iya gaskiyan ki meke tsakanin ki da kaninmu Sadiq? Domin hankalina ya tashi da naga wannan Hoton ina Fatan kada tunanin da na ke yi ya zama gaskiya." Bani da mafita sai na Fad'in gaskiyata, kuma na tabbata in ma na yi karya sai sun gane, tunda ga shi sun samu kyakyawan Hujja a garemu. Kaina na kasa ina sharan kwallah zuciyata Tuni naji ta tsinke, na amince zan fad'i gaskiyata ammh kuma zan rokesu Kada su rabani da Assadiq a Lokacin da zuciyata bazata iya Daukan Rabuwa da shi ba. Sajida cikin dakamim Tsawa tace"da ke fa ake mgana, malama kina bata mana Lokaci." Kawai sai na fashe musu da kuka, Surayya ta daga ma Sajida Hannu cikin bacin rai tace"Sajida kada ki kara mgana na gaya miki." Sai ta maida kallonta kaina cikin sigar lallashi tace"yi hakuri Hasiya,ki gayamin a ina kika san Sadiq? Kaina na kasa nace"Na san shi, Mi. MIJINA ne shi." Sajida ta Dafe kirji kafin tace"Mun shiga Uku miji kuma?. Ita kuma Surayya ina jin Sauke Ajiyar zuciyarta kamar na samun salama. Kafin tace"Har na tsawon wani lokaci kuke a matsayin ma'aurata? Cikin kuka nace"An fi shekaru uku." Surayya ta kalli Sajida itama ta kalleta cikin mamaki, a cikin Ran surayya sai da ta murmusa Sadiq Sadiq shegen gora ne. Wato tun zamanin ya na Hidimar kasa kenan, ya yi aure batare da kowa ya sani ba, gaskiya ya na da karfin Hali. Sajida kuma tsabar mamaki ma ya hanata mgana, ta bude baki yafi sau uku sai kuma ta Rufe domin ta kasa iya yin wata mgana. Surayya ta mike hannayenta goye a bayanta ta tsaya a gabana ta na fadin"Menene shaidar da zai sa mu tabbatar da gaskiyan mganar ku ma'aurata ne ba zaman banza ku ke yi ba.? Da Sauri na Dago ina kallonta kafin nace"Wlh ba zaman haramci mu ke yi ba, kowa a dangina yasan mun yi aure, kuma abokinsa ya sani sannan a gidan Baffan mu ma aka Daura mana aure." Surayya tace"Tahir? Sai na gyad'a mata kai, mirmishi ta yi daman tasan Tahir zai san komai Tunda ita dai bata san Sadiq da wani Amini  bayan Tahir ba, akwai tabbacin yasan komai daga Farko har karshe. Sajida ta kad'a harshe kafin tace"Shi yanzu Tahir da had'in bakin shi aka ci Amanar mu ko? Ba wansa ya tankata, ni ina ta kuka ita kuma Surayya ta na ta nazarin mganganuna. Kai Tsaye tace"Cikin jikin ki na shi ne? Sai na samu kaina da gyad'a mata kai, Shuru ta yi ta na kallona kafin ta koma ta zauna ta na fad'in"Me yasa kika amince kika auresa baki san Danginsa ba? Sannan kin zo gusai kenan hakan ya tabbatar min da cewa kin san ko mu su waye ko? Ina jan majina nace"Sai daga baya na san ku, ammh shi bai taba gayamin ba  asalima yace shi maraya ne ba shi da kowa sai kakarsa." Cikin mamaki Surayya tace"Bangane ba? Haka kurum naji ina son na gayamusu komai Tundaga Farko, sai kawai na gyara zama na fara ba su Labarin waceceni tundaga Farko Har karshe ban boye komai ba, Aurarranki da na yi tare da aurena da Assadiq da duk abunda ya faru, har Inplant din da Assadiq ya sakamin sai da na fad'a musu. Daga karshe na fad'i gaban Surayya na rike kafafunta ina kuka ina fad'in" Don girman Allah ku yi hakuri kada ku ce zaku rabani da Assadiq, in kuka rabamu ina zani? Baza mu iya rayuwa ba bu shi ba, da ni da abunda ke cikina." Na karishe fad'a cikin gunjin kuka, kamar zan shid'e da alamu  jikin Surayya ya yi sanyi, a ranta ta na Tunanin dama har yanzu akwai masu banzan Tunanin Canfe canfe, daman akwai mutanen da ke fuskanta Tozarci akan abunda ba su da masaniya a kan haka.? Ta kasa dago Hasiya, kamar wani shashe a ranta ya Tausayama Hasiya, sai kuma yanzu ta kara yarda da Dalilin Da yasa Sadiq ya aureta Tausayi ne da Taimako daga karshe kuma Allah ya rubuta da akwai Rabo da zama mai Tsawo a tsakaninsu. Sajida kuma ido kawai ta ke zarewa cikin Firgici ta ijiye yarinyarta a gefe ta mike ta na fad'in"Ki ka ce auran ki na Biyu Sadiq ne na uku? Mun shiga uku mun Lalace Taurin kan yaron nan ya sa ya jawo mana Mugun iri acikin zuru'a? ammh uwarki dai itace batulu duk alherin da ya yi mata sai ta saka masa da Sharrin Bin Rayuwarsa? Ai tasan ke Annoba ce meyasa ta nace sai ya aure ki? Wannan wlh zalumci ne, in wani abu ya samu dan'uwan mu na rantse da Allah sai Abba ya karar da duka Ahalin ku, matsiyatan banza kawai da Wofi." Ta fad'a cikin bacin rai, Surayya da ta daka mata tsawa cikin Fushi ta kira sunanta" Sajida." Sajida cikin fusata tace"Big sis ke baki hango abunda na hango ba ne? Sadiq kadai garemu yanzu in wani abu ya sameshi ya zamu yi? Kai Tsaye Surayya tace"Ba bu abunda zai same shi face abunda Allah ya tsara masa, da zai samesa da ya samesa Tuntuni, tunda ba yau suke tare ba, ki koma ki zauna ki kuma Rufemin bakin ki anan wajen" Sajida ta koma ta zauna ta na fad'in"Bazawara! Bazawara Kai ina wannan Had'in kwata kwata bai yi ba, da sake wlh" Ta fad'a ta na jin kamar ta Rufe Hasiya da duka, tsanar ta taji ta kara shiga ranta, daman tun jiya ta ke tsine mata tun kafim ma tasan abunda ke Tsakaninsu. Ina duke gaban Surayya ina kuka bani da tacewa domin nasan irin wannan Ranar ta na zuwa. Surayya ce ta saka Hannu ta Dagoni ta kuma mikar dani Tsaye ta zaunar dani saman kujera ta na fadin"Ki rage wannan kukan kin ga Halin da ki ke ciki ko? Fuskata Hawaye shabe shabe da hawaye da majina na kalleta ina fadin"Bazaku rabani da Assadiq ba ko? Sai kawai ta yi min mirmishi kafin tace"Bamu isa mu rabaki da mijin ki ba, tunda ai bamu muka had'a ku ba Allah ne, ki kwantar da Hankali in sha Allahu Alherinne zai Biyo baya." Ban san Surayya Sosai ba  ammh kuma sai naji na aminta da mganarta. Da tace na daina kuka sai na Daina na koma saka bayan Hannuna ina share hawaye. Sai da na natsu sannan Surayya tace"Duk da ina Babba  bani da ikon yanke komai a rayuwar Sadiq ya na da magabatansa, zamu koma gida zan sanar ma iyayensa, so na ke Sadiq ya Fahimci Babban Kuskuren da ya yi, na yi aure ba da sanin iyayensa ba." Sai ta d'an dakata ta na Kallona kafin tacigaba da fad'in"Hasiya ki kwantar da Hankalin ki, kema ba laifin ki ba ne ya zauna da ke da karya kamar yadda muma ya lullubemu cikin karya, ki yi min alfarma Rufe zuwan mu a matsayin sirri bazaki taba bari Sadiq ya sani ba kin ji ko? Sai na gyad'a mata kafin nace"Bazan gaya masa ba, daman kuma ina ta ce masa ya sanar da ku game dani, sai yace yana jiran Lokaci ne, abunda na ke tsoro kenan ko da yaushe ina cikin Fargaba, ina tsoron kada daga baya ku zo ku sani ku ki karb'a na ni da Abunda ke Cikina." " Ai ba zamu taba karb'an ki ba, Daga ke har shegen cikin jikin ki, da kike kokararin Dangantamu da shi, mu Sultana Kad'ai muka sani matar Dan'uwan mu, in dai ba ita bace ta haihu bazamu iya karb'an Datti acikin Zuru'armu ba." Sajida ta fad'i haka cikin Tsanar Hasiya har ya na bayyana a saman fuskarta, sai na kasa kallonta Saboda yadda naji kuka ya tasomin sai kawai nace"Ku yi hakuri don Allah, kada abunda ke cikina ya fuskanci hukuncin da ba laifin sa ba ne." Surayya ta balla ma Sajida Harara kafin tace"Wlh da na san abunda zaki yi kenan da ban zo da ke ba." Jin haka yasa Sajida ta yi shuru, ammh ta na ta kunkuni ita kad'ai. Surayya ta yi banza da ita, ta koma ta na kallona cikin sanyin murya tace"Kada ki damu Hasiya kin ji ko! Tunda har kun yi aure komai zai zo da sauki, ki rufe wannan mganar in muka koma gusai zan sanar da su Abba, kila akwai bukatar ki zo Gusai Domin tabbacin, zan baki lambar wayata in bukatar hakan yaa ta so Direban da ya kawomu zai zo ya Dauke ki kin ji ko? Cikin Tsoro na kalleta kafin nace"Assadiq fa? Surayya tace"Zai san komai Daga baya, kada ki damu ki yarda dani." Sai na kasa musa mata, wayarta ta Dauka ta yi danne danne. Sannan ta Dago ta na kallona kafin tace"Na kira ki da lambata, ki adanata zan kira ki in sha Allahu." Sai na bi ta da kallon mamaki ina ta samu lambata? Kamar ta sani sai ta fara min bayanin ta inda suga hoton da komai. Surayya ta ce"bamu sha wani wahalan gane gidan ba, tunda baya cikin lungu, sai dai mun shiga wani gida achan baya matar gidan ne tace mu zo nan ta na Tunanin ke ce'" Sai na kasa mgana ina kara jin Tsoron Rayuwa zaton abunda ba ka yi zato ba. Ko ni bansan Safiya ta Tura wannan Hoton ba, sannan bani da masaniyar yayarta khairiya na mu'amala da Daya daga cikin yan'uwan Assadiq. Surayya ce kad'ai ta sha ruwa  har na samu karfin halin cewa zan musu girki tace za su tafi ne ba wanda yasan sun yi wannan tafiyar. Har ga Allah sai naji Surayya ta Burgeni baki ta ke ta bani ta na lallashina akan na daina kuka ko Damuwa ta na da tabbacin Komai zai zo da sauki na kwantar da Hankalina Sajida ko da mun had'a ido sai ta harareni da kallon Tsana, daman nasan ba kowa ne zai karbi mganata ba, zan Fuskanci tarin kalubale. Tun ballatana da za su tafi, surayya ta rike hannayena ta na kallon cikin Idanuwana tace"Ki kwantar da Hankalinki Asiya, ba bu abunda zai Faru Sadiq kanina ne kuma Favorite d'ina, ya na ji dani, nima kuma ina ji da shi, kaf gidanmu ba shi da abokiyar shawara kamata, na yi mamakin da bai iya sanar da ni labarin ki ba, na yi masa uzurin Halinsa ne na Taimakon wanda ke neman taimako sai dai bazan taba masa uzurin boye mana wannan gagrumin abun ba, Tunda abu ne da ya shafi aure da Rayuwa gabadaya,so ki kwantar da Hankali komai zai wuce in sha Allahu." Sai naji hawaye sun cikamin kwarmin Idanuwana, na fara yi mata godiya tace min bakomai. Sannan ta yi ta jadaddamin na cire damuwa har ta na zolayata akan ina Dauke da Bbyn su, kada na yi musu asara sai ga shi ina Dariya. Sajida ko ta fita mota, saboda ta kasa zama gani ta ke yi kamar kunnuwan Surayya Hala sun toshene da ta tsaya tana Saurarena kuma har ta na Neman Goyen bayana. Suna tafiya na koma falo na zauna kan kujera, na saki kuka  ta wani bangaren in na duba Surayya sai naji kamar na samu salama, ta wani Fannin kuma in na Tuna ire iren su Sajida sai naji na Raunana, na Shiga uku ina zan saka kaina in har Assadiq ya rabu da ni? Na tabbata Rayuwata sai ta fi baya kuntata matukar haka ya faru. Surayya da Sajida a kan hanyarsu ta komawa Gusai, Direba na gidan gaba ya na Tuki su kuma suna gidan Baya, Surayya ko mijinta bata gayama gaskiya ba,  Sai cewa ta yi Umma ce ta aiketa Sajida kuma zata rakata. Kowannensu ya yi Shuru zuciyarsu na saka musu tunani iri iri. Surayya tunaninta ya zurfafa sannan ba irin na kowa ba ne, Damuwarta daya ne yadda su Umma za su Karb'i mganar uwa uba kuma Innani tasan akwai babban kalubale, ballatana su san Labarin Hasiya, sannan ta ga alamun za su kyamaceta jin ita bazawara ce, sannan ga Sultana bata san ta ina zasu Karb'i mganar ba. Ba ta jin Abba shi ya na da Saukin kai, Umma ce abun ji saboda ba lalle ta yarda da abunda zataji ko zata gani ba. Sadiq ya yi kuskure kuma ya zama Dole a nuna masa rashin kyautawarsa, sai a yanzu abubuwa ke dawowa kanta daki daki ta tuna yadda aka sha fama da shi kan auran Sultana tun a wanchan lokaci ashe ashe ya na dalilinsa, daman ita fa ta yi wannan Hasashen na cewa akwai wani abu a zariyan nan da ya ke Dauke ma Assadiq Hankali, ta kira Tahir ta tambayeshi ya yi mata karya shima, ta na mamakin Wayau Sadiq har ya iya yin aure a boye ya kama ma matar haya suna zaune tare, har tsawon wannan Lokacin ba wanda ya sani abun a jinjina masa ne. A gefe daya kuma na zuciyarta tausayin Hasiya ya darsun mata, Ba laifinta ba ne ammh sai ga shi ta na Shiga gagarin rayuwa saboda hakan, sannan har itama Sadiq ya yaudareta Don ma zuciyar macece da Rauni Sannan Tsskanin mata da miji sai Allah, ammh ai ko ta barayin hanata Haihuwa yaci Amanarta, ammh ko ma menene Allah ya nuna isharansa shi ya Kulla auran su, kuma shi ya nuna cewa akwai zuru'a a tsakaninsu. Tunanin ta ya na tafiya ne kan yadda zata iya gayama Umma da Abba wannan Labarin. Ba Sadiq zata taimaka ba, Hasiya ce wacce taji matukar Tausayinta ta na cikin wani Halin da ta ke Bukatar taimako, Sadiq kuma chan ya karata Shi da ya kira ruwa shi ruwa zai Cinye, zata dai Tsaya tsayin daka ta ga an yi ma Hasiya adalci ko domin cikin Sadiq da ke jikinta. Ammh tabbas sai ya karb'i Hukuncin abunda ya aikata, sai ya gane ba shi da wayau bazata yarda ta karesa ba, Gwara ya gane kuskurensa nan gaba bazai kara gigin aikata haka ba. Sajida ko acikin ranta ta gama kissima, irin yadda zata zuga Umma da Innani, in sha Allahu wannan bakar Annobar bazata zauna acikin zuru'arau ba. Sadiq kuma ta zageshi a ranta bata san iyakata ba, Shege bata san Uban me ya gani a jikin wannan yarinyar ba farinta kamar na ma su cuta, ta gama tsara har Sultana sai taji mganar nan kuma zata zugata tace bazata zauna da Sadiq ba sai ya saki wannan Annobar. Surayya kamar tasan Tunanin Sajida ta kalleta ta na fadin"Sajida kada naji mganar zuwan mu zariya a bakin kowa, Saddiqa kawai zata ji itama Saboda tasan mganar ne, ammh ban da Labarin Rayuwar Hasiya na baya Sajida ko a gida bazan fad'a ma su Umma canfin karyan nan da mutane ke yi a kanta ba, domin ni kaina ban yarda ba, sai dai ba laifin in sun ji cewa a bazawara ya aureta." Sajida ta kalleta Sheke sheke kafin tace"Meyasa ba za su san abunda Sadiq ya kawo mana cikin zuru'a ba? Big sis ki yi hakuri duka sai na karanta ma yan'uwa da su Umma gwara su san abunda ke Faruwa, kina fa ji da bakinta tace duk wanda ta aura ko rasa dukiya ko rasa lafiya, Sadiq kadai ne garemu namiji in wani abu ya same shi ba? kuma mun sani muka Boye wlh Allah bazai barmu ba, ni dai ba Ruwana bazan iya Boye wannan mganar ba ki yi hakuri." Sai Surayya ta kasa mgana ta na kallon Sajida jin ta kara cewa"Kuma banda Sadiq ya yi asara me zai ci da auran bazawara? Bazawaran ma wacce ta yi aure Har biyu, abun takaicin ma  kuma yasan komai a kanta ammh kuma ya aureta a haka ba da sanin iyayensa  ba Dan Burauba ai ya yi asara wlh, ina sultana zata had'u da wannnan matar? Fatar jikinta kamar na mayu, har ga Allah ban ga abun so a jikinta ba sai wauta irin ta Sadiq." Ran Surayya ya baci da Sauri tace"Ya isa Sajida, kar ki Rufa asirin kin Dad'e baki Tona ba, ammh ki saani wanda ya Rufa ma wani asiri shima Allah zai Rufa masa asiri ranar gobe kiyama, kuma da ki ke mganar bazawara kina Zagin dan'uwan ki, kin san adadin ladan da ya samu akan haka? Ba zaman bariki ya ke yi da ita ba Matar aurensa ce da shaidu suka shaida auran su, kinga kuwa ko wannan kadai ya isa ki yi salama ki kuma jinjina hikimar Ubangiji" Sajida ta kyabe baki kafin tace"Daman Tun a dazun na Fuskanci zaki goyama Sadiq da yarinyar nan baya kamar yadda kika saba tsaya masa, ammh ina so ki sani ko Umma bazata taba karb'an wannan yarinyar da abunda ke Cikinta ba." Surayya tace"Ni ba su zan tsayama ba, Ina bayan gaskiya ne, domin ita ba namu ba ne hakan baya nufin bazamu yi mata adalci ba, itama in zamu kalli abunda ta Fuskar adalci ya yaudareta kamar yadda mu ma ya yaudaremu, maganar Annoba da kike fad'i ki bari Allah ne ya Halliceta tare da kaddaranta ki daina Dariyann rayuwarta ke kuma kina alfahari da naki Rayuwar, mganar bazawara kuma kada ki zama Jahila Sajida, da ilimin ki da komai, ki ke so ki kawo wani karatu na banza wani nafsin ne yace ita bazawara ba Mutum ba ne? Ko kuma akace Saurayi ba zai iya auran bazawara ba? Kin manta da Labarin Annabi ne da Nana khadija? Ashe ko in da shi mu ke ko yi, mu al'ummarsa bamu isa mu kyamaci bazawara ba." Sai ta yi shuru ta dakata, ta na lura da Sajida da ta koma ba ma yaronta Nono, kanta na gefe kamar maganar na Surayya ta na shiga ne ta na fita. Ganin haka yasa Surayya ta Had'e rai kafin ta cigaba da fadin"kuma da ki ke mganar Umma bazata amince ba, daman bukatar shi ne a bi kadin auran a tabbatar da auran na gaskiya ne, bayan wannan ruwan kowa ne ya karb'i Asiya ko kada ya karb'eta ammh baku isa ku sauya wannan mganar na cewa itace Matar Sadiq ta farko, sannan har Abada ita din iyalinsa kinga shaida ma, tunda ga ciki kin gani a jikinta,ni bazan kara miki magiyan ki kama bakin ki ba, ammh ina so ki sani, ita Rayuwa ta na da Fad'i, kila watarana Asiya zata iya miki wani amfani ta fanni da baki zata ba, ko da ki ke ganin kin rainata." Daga haka ta kama bakinta, ta koma ta na kallon tagar gefenta ta na ganin Dajukam da suke wucewa. Sajida kuma ko a ranta ba ta ji zata iya Rufe wannan mganar ba, kuma har acikin ranta bata hango Sadiq ya cigaba da zama da wannan yarinyar ba. Ta na jin Surayya na magana da Saddiqa ta na kara bata tabbacin da gaske ne Hasiya matar Sadiq ne ita ya fara aura a boye kafin ya auri Sultana, Dagachan Bangaren Saddiqa ta na ta salati, Sai dai surayya tace ta bari su koma gida za su tattauna yadda za su tari su Abba da mganar, ammh ko ita tace kada sauran su ji tukunna dai. Wajen la'asar suka isa Gusai, har gida Surayya suka kai Sajida sannan Suka wuce gidanta. Daren ranar ta kwana Tunanim mafitan yadda zata kai mganar nan gida ta kasa, wazhegari da Safe sai ga kiran Sadiq bayan ta Dauka sun gaisa bata nuna masa komai ba. Sai yace zai shigo wannan Satin in ta na Free akwai mganar da za su yi. Sai Surayya ta zargi ko daman shine maganar da ya kasa fad'a mata? Sai ya ba ta Tausayi, da Sauri tace"Ina nan Sadiq, wannan wani irin mganace tun yaushe ka ke cewa zamu yita, ka kasa kuma fad'amin? Ina fatan dai lafiya ko? Dagachan Bangaren Sadiq ya yi shuru kafin yace"Sai dai na zo big sis, ina fatan zaki fahimceni kamar yadda kika saba Fahimtata a baya." Sai kawai Surayya taji kwalla ta cika Idanuwamta, sai tace ta na tsumayinsa. Shi kuma a satin Zariya ya kamata yaje, ammh ya riga ya yi kudurin Fad'ama surayya komai a kan Hasiya, sai ya kirata yace ta yi masa Hakuri yaje Gusai kan mganarta. Ni kaina ya na gayamin ina share kwallah, bazan iya gayamasa ya yi jinkiri ba, ballatana na sanar da shi abunda ya ke so yaje ya fad'a sun san da shi kafin shi ya Furta musu. Alkwarin da na yi ma Surayya na bazan fad'a masa komai ba yasa na kasa gayamasa komai. Sai dai ina ta addu'an Allah yasa koma me zai Faru ya zo da sauki. Sadiq yaje gusai, ammh kana ganinsa wani sukusuku, Sultana duk yadda ta Shiryamasa Tarba ya kasa sakin jiki, kuma har ita kanta bai wani yi mata rawan jiki da ya kan yi in ya zo ba. A daran jumma'an duk yadda ta so su kad'aice bai biye mata ba, sai yace mata baya jin dadi, washegari kuma da Safe yaje gaida su Umma. Ita kanta Ta Fahimci ya rage walwala ta tambayesa ko lafiya? Sai yace gajiyan aiki ne. Abba ma sai da yace ko ya yi ciwo ne?Sai yace a'a, Abba kai Tsaye yace yaga ya rame ne, kuma ya rage walwala. Sai ya kasa mgana, Daga Shashen Innani gidan Surayya yaje, sai dai duk kokarinsa da mganganun da ya gama Tsarawa ya kasa fad'a ma Surayya su  kuma bayan ita ba shi da wani Sauran Hope. Zaune kawai ya yi tsuru a gabanta, ya kasa magana ya rasa ta ina ma zai fara, duk abunda ya shirya ganinsa gaban Surayya sai yaji komai kamar an shafe masa daga kwakwalwarsa. Surayya ta kallesa shuru ta na nazarinsa, kafin tace"Sadiq me ke faruwa ne? Tun dazu ka yi shuru ka kasa mgana? Sadiq ya runtse ido sannan ya Bude ya kasa had'a ido da ita, cikin jin nauyi da kunya yace"Big sis na rasa ta ina zan fara ne" Da sauri tace"Ka fara ko ta ina Sadiq, zan fahimce ka." Ta fad'a ta na fatan ya fad'a mata da bakinsa. Ammh Sadiq ya kasa, ce mata kawai ya ke yi"Big sis na yi muku Laifi, a lokacin wlh zuciyata ba ta ganin komai sai na taimako, ku yafe min." Surayya ta kallesa kafin tace"Me ya faru? Ka gayamin don Allah" A gefe daya kuma daga shi har Hasiya suka bata Tausayi domin ta hango Tsaka mai wuyar da za su shiga. Ammh abun Takaici Sadiq tafiya ya yi, batare da iya gayama Surayya komai ba, ya dai ce kawai yaci amanarsu su yafe masa. Kasa fad'a mata ya yi, yace zai dawo gobe ya na tafiya sai ga  wayar Saddiqa, Surayya ta karanta mata yadda suka yi da Sadiq. Saddiq tace"Wayyo Sadiq ya shiga Tsaka mai wuya, ni kaina ina fatan su Umma su Fahimcesa." Surayya ta so ta kara Turke Sadiq in ya gayamata sai ta gayamasa komai ta kuma nuna masa kuskurensa ta yi masa adalci bisa gayamata da ya yi. Ammh sai me? Ta yi ta kiran wayarsa bata samu sai ta kira Sultana, ita ke gayamata ya tafi zariya yau da safe dagachan zai wuce Abuja. Surayya ta sauke numfashi, Sadiq me yasa ya ke haka ne? Wannan fa gudun nasa ba mafita ba ne. A ranar ta gama yanke shawaran abunda zata yi, ya kamata zuwa yanzu su Umma su san abunda ke faruwa. Ba sai na nesa sun zo ba, ko da iya na kusa ne sun wadatar, Saddiq ta kira suka yi mgana, ta tabbatar mata da zuwa Jibi zata zo sai su taru su sanar da ma su Umma komai cikin Rukuni. Ba ta yi ta kan Sajida ba ta lura so ta ke yi ta b'ata al'amarin to gwara tun kafin ta bata lamarin ita ta warware komai. Sun rabu da Saddiqa akan Surayya zata Tura ma Hasiya Direba gobe ko jibin ya kawota gidanta ta kwana ranar Laraba da zasu taru sai ta taho da ita hakan zai fi sauki. Bata kirani a ranar ba sai Ranar Litini da safe, lokacin ina makaranta Assadiq ya saukeni ya wuce Abuja. A yadda ya zo min na yarda cewa yan'uwansa ba su fasa mganar ba. Ammh mun rabu bayan ya tabbatar min da cikin Satin nan zai fad'ama Ahalinsa komai game da ni. Bayan mun gaisa kai Tsaye surayya tace"Sadiq ya tafi ko ya na nan? Cikin jin nauyi nace"Dazu da safe ya wuce." Sai tace"Ki shirya zuwa gobe zan aiko Direba zai taho da ke wajena, ki shirya kayanki kamar kala uuku haka" Cikin wani yanayi nace"Ba matsala ko Anty Surayya? Da sauri tace"In sha Allahu, zan kira ki in zai taho." Daga haka muka rabu, a cikin raina sai nake jin wani Tsoro. Tsoron abunda zan je na tarar, abu biyu ne ko su aminta dani ma zauna cikin Tozarci ko kuma su rab'a ni da Assadiq sun yi min koran wulakanci. In hakan ko ya faru na lalace domim bansan kuma wani mafita zan kama ba. *Janafty* *TMWBK3005* *TMW is a paid Novel, Pay 500 for regular or VIP N1K, Via 0552179550 Jamila Umar Gt bank, 09069067488* https://chat.whatsapp.com/BARBh2begGc0KdlLEZDzhk Ku zo ku yi sayayya tare da Yar Gidan Imam cikin aminci da kwanciyar hankali komai akwai harda kayan gyaran jiki hamshakan mata na supliments kala kala wanda ba su da illa, akwai kuma gagarumin haɗin mu na Arabian sabaya powder wanda babu kamarsa wannan ba irin sabayar da ki ka saba gani bace, kayan kicin dogayen riguna kuwa ba'a magana ke dai ki yi sauri ki shigo domin kwasar roman wadannan kayan. Washegarin Talata Saddiqa ta baro Kebbi zuwa Gusau, kuma ita kad'ai tazo ba tare da yara ba tace saboda makaranta sai ta barsu a gida tare da Babansu. Zuwan bazata tayi, tunda ko Umma sai dai ta ganta kwatsam gashi motar haya ta shigo ta sha wuya, ammh abun mamaki ta na isowa sallolin da suka Subuce mata ta fara rankawa kafin ta ci abinci. Ta na gama cin abincin sallar mangariba tayi, tace ma Umma zata je gidan Surayyah abun sai ya ba ma Umma mamaki, ganin ko hutawa ba tayi ba, kuma tace zata fita. Taga kuma ko shashen Mama bata je ba, ta dai Leka shashen innani sun gaisa gashi ma Abba bai dawo ba. Umma ta kalli Saddiqa na waya da megidanta, tana nazarinta sai taga kamar zuwan nata ya sha bambam da zuwan da ta saba yi, daga gani tafiyar tazo ne babu shiri. Jin kuma tace zata je wajen Surayya da Daren nan, sai gabanta ya fad'i ta fara Tunanin ko wani matsala ne ya faru da Surayyan ba su sani? Tunda ta kwana Biyu bata leko su ba, Umman ce ma ta kirata shekaranjiya sai taji muryanta wani iri, da ta yi mata mgana sai tace bata jin dadi ne. Saddiqa ce ta katse ma Umma Tunani da cewa"Umma bari naje, kada na yi dare na rasa abun hawa." Umma ta sauke ajiyar zuciya kafin tace"Saddiqa Surayyan ta na lafiya kuwa?  naga daga zuwan ki, baki huta ba kuma kin ce zaki tafi gidan Surayya" Da sauri Saddiqa tace"Lafiya kalau fa, kawai ina so naje akwai mganar da zamu yi ne, kuma ba dadewa zan yi ba kila jibi zan koma." Kamar Umma zata kara mgana sai kuma ta fasa, sai kawai ta ce "Allah ya kiyaye hanya, ki kwana achan kawai in dare ya yi." Saddiqa na daukan wayanta da Jakarta na Hannu tace"Zan dawo Umma ai Bamu gaisa da Abba ba." Ba'a son ran Umma Saddiqa ta tafi ba  ta na fita Haraban suka had'u da Mama zata zo shashen Umma suka gaisa itama da tace mata zata je gidan Surayya sai da ta kalleta kafin tace"Da daddaren nan Saddiqa? Allah yasa lafiya" Saddiqa tace"lafiya lau Mama, bari dai naje ba dad'ewa zan yi ba." Daga haka suka rabu, adaidaita ta samu zuwa gidan Surayya, Daman sun yi waya dazu da rana lokacin suna hanya ba ta riga ta iso ba. Surayya na falonta zaune ita da yaranta suna homework sai ga Saddiqa cikin mamaki ta mike ta na fad'in"Saddiqa" Cikin irin nayi mamakin ganinki a yanzu. Saddiqa ta samu kujera ta zauna yaran Surraya suna gaisheta, karamar ta dauka saman jikinta Lokaci d'aya ta na fad'in"Ban dad'e da isowa ba, nace sai nazo ina so mu yi mgana, big sis ta na zamu fara kamo bakin zaren wannan maganar nan? Surayya ta kalli yaranta lokaci d'aya ta na fad'in"ku shiga ciki khalil." Sai da suka shiga cikin sannan ta mike ta na fad'in"Bari na kawo miki lemu da ruwa." Saddiqa tace"Bar ruwan nan Big sis, ki zo mu zauna mu yi mgana." Ba musu surayya ta dawo gefen Saddiqa ta zauna ta na fad'in"Ina jinki Saddiqa, ta ina ki ke ganin zamu fara? Saddiqa na fuskantar ta lokaci d'aya ta na fad'in"big sis ni a shawarata ta inda aka hau ta nan za'a sauka." Surayya tace"Kamar ya? Saddiqa ta gyara zama ta na fad'in" Nufina anan shine Sadiq ne ya jawo komai saboda haka shi sai ya zo ya sanar ma su Umma da bakinsa, in muka Shiga fad'an da babu ruwan mu  fa? Kuma abun haushin ma ba da bakinsa ya fad'a mana ba, shi har yanzu bai samu lokacin sanin bai kyauta gamw da abunda ya aikata ba." Surayya ta yi shuru kafin tace"Ban ki ta mganarki ba, ammh ni a shawarata tunda kin zo, ni da ke zamu tara su Umma mu sanar da su abunda ke faruwa." Saddiqa ta zaro ido kafin tace"Mu kuma?saboda mene? Surayya ta gyara zama lokaci d'aya ta na fad'in"Saboda Sadiq kanin mu ne." Saddiqa ta katsesta da fad'in"Kina so ki nuna min zamu kare Sadiq a wajen su Umma? Zamu karesa big sis ki ke nufi duk a irin abunda ya aikata? Tabdijan wlh in muka yi haka ma gobe sai ya kara  ya ma raina mutane wlh" Saddiqa ta karishe fad'a ta na Nuna bacin ranta kafin ta cigaba da fad'in"kuma suma su Umman ai su gani, tsabar soyayyar da suka nuna ma yaron nan da Abba da Innani, suna Fifita mganar Sadiq a saman ta su, ba dole ya je ya aikata abu mai girma haka bada sanin kowa ba, ya na Tunanin babu abunda zai faru ne shiyasa kika ga ya yi shurunsa ko ajikinsa fa." Surayya ta yi mirmishi ba ta yi mgana ba, Saboda ta na Tunanin ba lalle in ta yi mgana kowa ya fahimceta ba. Sanin tsakaninta da Sadiq yanzu sai ace shi ta ke goyama baya. Tana cikin wannan Tunanin taji Saddiqa na kara fad'in"Nasan dai tsakanin ku da Sadiq akwai kauna, kin fi shakuwa da shi duk da yana namiji, ammh bai kamata ki goyamasa baya ba, tunda duk yadda ku ke bai iya samun ki ya fad'a miki ba." Surayya ta kara yin mirmishi kafin ta muskuta ta na fad'in"Ke ma kina Tunanin ina Goyon bayan abunda Sadiq ya aikata ne? Saddiqa tace"Haka ne mana, tunda kina so ya na chan kwance mu mu yi masa yakin a nan." Surayya tace"Ba shi zamu yi ma yaki ba, Adalci zamu nema ma Hasiya." Saddiqa ta yi karamin Tsaki kafin tace"Wacece wata Hasiya kuma? Chan ita ta sani, me ya kaita auran wanda bata sani ba? Surayya tace"Kada ki manta itama ya yi mata karya, in zamu kalli abun ta fuskar adalci itama bai kyauta mata ba. Kuma ni wlh tallahi bazan kare Sadiq ko na minti d'aya a gaban su Umma ba, Hasiya da na yi ma alkwarin komai zai yi daidai ita zan nema ma adalci. Saddiq sai kawai ta tab'e baki ta na kallon Surayya kafin tace"Ni bangane manufar manganunki ba, yanzu kina so mu je ma su Umma da mganar sannan mu tsaya ma matar da Sadiq d'in ya aura ko me kike nufi? Surayya tace"A'a abunda na ke so mu yi shine, mu sanar da su Umma saboda su san halin da ake ciki." Saddiqa tace"To shi me yasa in ya gane ya yi ba daidai ba  bai zo ya fad'a da kansa ba? Ko ba shi da baki ne? Surayya tace"Sadiq na cikin Tsaka mai wuya, ko ni duk yadda mu ke da shi wlh saddiqa ya kasa fad'amin, nan yazo ya zauna ammh ya kasa iya fad'amin komai." Saddiqa zata yi mgana Surayya ta yi saurin Dafa kafad'arta ta na fad'in"Ki yi hakuri  na yi miki alkwarin ko sau daya bazan boye laifin Sadiq ba  ammh ni dai ki tayani sanar da su Umma komai." Saddiqa ta kalleta a kaikace, itama sai ta langwabar da kanta ta na kara fad'in"Ban san ki da haka ba Saddiqa." Ajiyar zuciya ta sauke kafin tace"Shikenan domin kin matsa ne, ammh wlh ni naso ki bari sai matar ta Haihu, naga yadda zai kare, yaro karami ammh ya iya raina ma mutane Hankali." Surayya ta yi dariya ta na fadin"Ba yaro ba ne karami, namiji  ne shi kada ki manta." Saddiqa tace"Hakane yanzu na Tabbatar da haka." Sun cigaba Tattauna yadda gobe surayya zata zo domin su sanar da su Umma Halin da ake ciki. Maganar Dauko Hasiya kuma Saddiqa ta ba da shawaran su dakata su yi mgana da su Umma su gani, yadda suka karbi mganar ta yanayin da za su  samu mafita kenan. Surayya ta gyad'a kai alamu gamsuwa kafin tace"To shikenan Allah ya kaimu, ina fatan komai ya daidaita in sha Allahu." Saddiqa tace"Ammh ki kira yaron nan, mu zamu kwanto masa kuran da ya Daure, sai ya zo ya san yadda zai yi ya sake Daureta." Surayya ta saka Dariya kafin tace"Zan kirasa ai mganar boye boye kuma ta kare masa." Sun cigaba da Tattaunawa har Mijin Surayya ya Dawo, shi kanshi da ya ga Saddiqa ya sha mamaki har yana yi mata tsiyan hausanta ya koma na Sokkatawa. Karfe goma da wani abu Surayya da Mijinta suka dawo da ita gida ba su shiga ba a kofar gida suka sauketa suka rabu akan sai gobe. Umma sai da ta ga Saddiqa ta dawo ta ga ba wani abu sannan Hankalinta ya kwanta. Yadda Saddiqa bata ce mata ba, itama bata matsa mata da mgana ba. Abba ma sai da safe taje ya ganta suka gaisa saboda a daran Mama ke da Turaka kuma dare ya yi shiyasa bata shiga ba  ammh tasan tabbas yasan da Labarin zuwanta. Da safen ma da taje gaishesa sai da ya tambayeta lafiya ko? Tace masa lafiya Lau tazo ganinsu ne, ta jima a wajensa suna Hira,  saboda Abba mutum ne da ke sakewa da ya'yansa. Daganan sai shashen Mama, itama sun jima suna Hira da ta ga falon wayam ne ba kowa yasa tace"Shikenan gida ya zama tsit, Siyama ta zama yar gidan Sadiq." Mama na dariya tace"Wlh gida fa ya yi tsit ba kowa, to sai farida ita kuma ta na barayin Innani, in kin ganta anan sai in aikota ta yi Siyama ai sai Sadiq ya dawo ki ke ganinta a gidan nan, in kuma baya nan sai dai su zo tare da sultana." Saddiqa tace"Itama Allah ya kawo mata miji nagari ta yi auranta." Mama ta amsa da Amin sun cigaba da Hiran Salima wacce Mama ke fadin yanzu bata zama sosai tunda ta fara karatun nan. Sai da Saddiqa ta koma Shashen Umma sannan ta kira Surayya, nan ta ke fad'a mata ta kira Abba tace kada ya fita zata zo akwai maganar da ta ke so su yi da shi, sai yace daman yau ba da wuri zai fita ba sai an juma. Sun Tsaida mganar Daga Umma sai Abba sai mama da Innani za su yi mgana daga baya in komai ya daidaita sai mganar ta fita ga sauran yan'uwa. Tunda Surayya ko Sajida bata nema ba  a wannan karon ba Hurumin su ba ne. Da wuri Surayya ta zo gidan Umma dai mamaki sai ya kamata tun ballatana da taga sun kule a daki ita da Saddiqa, da kuma sun ganta ta shigo sai su yi tsuru tsuru, Umma dai ta na kallonsu a ranta ta tabbatar akwai wani abu, tunda ta shiga su gaisa da Abba ya ke gayamata wayar da suka yi da Surayya. Gabanta ke fad'i fatan ta d'aya Allah yasa ba wani abu na mara kyau ya samu d'aya daga cikin yaran ba. Zuciyar Uwa duk sai ta firgice zullumi ya shiga ranta duk sai ta kasa sukuni. Surayya da kanta taje Bangaren Innani bayan sun gaisa sun taba Hira, Innani na bata labarin Farida mai kirki ga ba ta da kiyuwa ba kamar su Siyama ba. Har Innani na fad'in ba ta yi Halin uwarta ba, Surraya dai na jinta ta na faman dariya. Da ta ga Hiran ta ki karewa ne yasa tace ma Innani zata rakata bangaran Abba za su yi mgana ne. Innani ta karkace kai kafin tace"Shi Sulaimanun ne don zai yi mgana da ni, sai na je da kaina? Surayya sai ta kasa mgana Innani ta fara masifa ta na fad'in"Shi kuma Sulaimanu lalacewa ne ko bakin duniya ce ta fara kamasa da ni ina uwarsa zai ce sai naje da kaina har bangaransa? Naga dai daga shi har matansa nan suke zuwa su tarar da ni, ko da suna da mgana da ni." Sai Surayya ta Fahimci kuskurenta da Sauri tace"Yi hakuri Innani , bari mu muzo sai a yi mganar a nan bangaren." Innani ta tabe baki kafin tace"Da dai yafi muku." Dole Surayya ta koma ta fad'ama Saddiqa yadda suka yi da Innani, sai Saddiqa tace ba matsala sai ayi achan din. Surayya ce tace ma Umma su je bangaren Innani su yi magana, Umma bata ce komai ba illah tace to kawai, Ita Mama Saddiqa ta je ta fad'a mata itama cikin mamaki tace lafiya? Saddiq tace suna fatan haka. Abba daman ba shi da matsala shi ya fara ma isa bangaren Innani, ko da su Umma suka zo sun iske su suna Hira na Tsakanin uwa da abunda ta Haifa. Ga dai Umma ga Mama ga Abba sai Surayya da Saddiqa ga Innani a gefe wajen mintuna goma falon ya Dauki Shuru ammh tsakanin Surayya da Saddiqa an rasa me fara cewa wani abu. Sai da suka zo gabansu Umma suka ji sun sare, barin ma Surayya da ta zo da kwarin gwiwanta, Saddiqa kuma Daman tace ita bazata fara mgana ba tunda Surayya ta karb'i fad'an ita zata san yadda zata yi. Innani ta gaji da zama sai ta kawai ta gyara zama ta na fadin"Wai me ya faru ne? Naga kowanne ya zauna ya yi shuru ko an yi mutuwa ne? Abba ya yi gyaran murya kafin yace"Innani daman Surayya ce ke son magana damu kan wani batu da bamu sani ba" Innani ta yi karamin tsaki kafin tace"Shine kuma ta taramu kamar wasu sa'anninta ta tsaya ta na kare mana kallo? Da Sauri Mama tace"Ki yi hakuri Innani, ke kuma babbar yaya muna sauraranki Allah yasa lafiya, ni wlh kada ku kasheni da zullumin me ke faruwa? Umma ta kad'a kai kafin tace"Wlh nima baki ji zuciyata ba, gabadaya na kasa sukuni don Allah ku fad'amana Abunda ke faruwa." Surayya ta kalli Saddiqa itama ta kalleta, Saddiqa ta tsinguleta alamun ta fara mgana, Dakyar Surayya ta iya jarumtar fad'in"Umma Abba, Mama Innani, magana ce a bakina sai dai yadda zan fad'eta ne kuma ku fahimceta shine Fargabata." Mama tace"Topha? Muna sauraranki in sha Allahu kuma zamu Fahimceki." Surayya ta Sauke ajiyar zuciya kafin tace"Dama. dama akan maganar Sadiq ne." Gabadayansu a tare cikin firgici suka Had'a baki wajen kiran sunan Sadiq. Cikin tashin Hankali Abba yace"Me ya faru da Abubakar din? Umma kuma da jikinta ke rawa da Sauri tace"Surayya ki fad'amin me yasamu Sadiq ne kada zuciyata ta Buga." Mama kuma sai salati ta ke yi, Innani kuma kuka kawai ta saka ta na fadin"Mun shiga uku mun lalace wani mugun abun ne ya sama mar min jika na? Namiji kwara d'aya da Sulaimanu ya mallaka magajin wannan gidan mijin sulsana mun shige su, me ya same shi? Ko mutuwa ya yi ne ku ke boyemana achan Habujan? Innani ta karishe fad'a cikin Ihun kuka. Jin maganar Mutuwa da kuma yanayin Rudewarsu yasa Da Sauri Saddiqa tace"Ba fa maganar Mutuwa ba ce ko wani abu, Lafiyan Sadiq kalau babu abunda ya same shi." A tare Umma da Abba suka Sauke Numfashi  mama ko sai da tayi hamdala. Innani ne ta tsaya da kukanta ta na kallon su Surayya ta cikin gilashinta na wani lokaci kafin a fusace tace"To karya ku ke yi, in ba wani abu ya sameshi ba uban me yasa baku fad'i abunda ya faru ba tun dazu? Kun tsaya kuna ta raina mana wayau.' Ta karishe fad'a cikin masifa, Abba dai jikinsa gabadaya ya yi sanyin da ya kasa mgana. Umma kuma zuciyarta ne taji ya na gudu sosai kamar dai wacce wani abu ya sameta. Cikin karfin hali tace"Zaku fad'a mana ne, ko kuwa sai mun mutu da zullumi.? Da Sauri Saddiqa tace"Sadiq ne ya yi aure Umma." Gabadaya sai falon ya yi shuru kowa na auna mganar Saddiqa. Innani ce ta yi tsaki kafin tace"Ji wani shashanci daman ai kowa yasan magajin gida ya yi aure, daman dalilin dayasa ku ka taramu anan kenan? Kai sulaimanu yi tafiyarka sabgoginka yara nan wasa za su yi da Tunanimmu." Surayya ta sauke ajiyar zuciya kafin tace"Innani ba wannan auren ba, kafin.. kafin ya auri Sultana to daman ya auri wata achan zariya." Sai falon ya kara Daukan Shuru Surayya kawai a ke kallo. Umma ta sandare a zaune, Innani kuma har gilashinta ta cire ta kara maidawa ta kara gyara kunnuwanta kafin ta kalli Abba ta na fad'in"Sulaimanu ko dai kunnuwana sun samu matsala ne? Me nake ji Ana fad'a na wai? Abba ya yi shuru bai ce komai ba, Mama ce ta kalli su Surayya cikin rawan baki tace"Ku yi mana karin bayani, bangane ba wani irin aure kuma? Surayya kanta na kasa tace"Aure ya yi a garin Zariya tun Lokacin ya na bautar kasa, shekaru uku da suka wuce." Mama ta Bud'e baki cikim mamaki kafin tace"Da gaske ku ke yi? Wani irin aure kuma ni Saratu? Saddiqa ta gyara zama ta fara ba su labarin yadda akayi suka ga hoton Sadiq da Hasiya da yadda suka Bincika suka gano gaskiya da zuwan Surayya zariya ita da Sajida. Da kuma karin tabbaci daga bakin Hasiya tare da Shaidar ma cikin jikinta. Mama ta koma ta yi zaman dirshan a inda ta ke  maimaitawa ikon Allah kawai ta ke yi. Umma kuma kanta na kasa bata Dago ba, ammh a cikin kasan ranta mamaki ne da al'ajabi Abba kuma ba wanda zai iya cewa ga yanayin da ya shiga. Innani kuma shuru tayi kamar bata ma afalon Inaga tsabar Mamaki ne ya hanata mgana wannan karon. Abba ne ya yi gyaran murya kafin yace"Shi Sadiq din baisan kun san labarin ya yi Auran ba? Surayya tace"Eh Abba, ya yi kokarin ya fad'amin ammh kuma ya kasa, daman tunda abun har ya fallasa naga ya kamata ku fara sani." Abba ya jinjina kai kafin yace"Ita matar tace Tahir ya san da mganar auran? Surayya tace"Tabbas haka ta ce ya sani" Kafin Abba ya yi wata magana Umma ta d'ago ta na kallon Surayya cikin wani yanayi kafin tace"Shi Sadiq din da kansa ya yi aure batare da sanin mu ba? Tsakanin Surayya da Saddiqa sai aka rasa me bama Umma amsa. Mama ce ta rike hab'a kafin tace"Ni kaina ina ta mamaki, Sadiq fa? Me yasa Sadiq da hankalinsa da Tunaninsa da iliminsa sai ya aikata haka? Aure fa kuka ce? Kuma kun ce an dade ma tunda su Surayya sun je sun ganta har da ciki" Kafin kowa ya samu zarafin mgana sai sai ihu da kurruwan innani suka ji, har ta na wani tuma da kafafunta kamar karamar yarinya. Cikin kuka ta ke fad'in"Wai daman da gaske kuke yi Magajin gida ya auri wata matar kafin sulsana? Yanzu Amana ta zai ci ya yi ma Jikata kishiya? Magajin gida ina ganinsa mai Hankali ashe maci amana ne, mara Mutumci to billahillazi bai isa ba, ya yi kad'an jikata ta zauna da kishiya ni da Magajin gida baram baram ko ya saki wacce ya aura ya zauna da jikata ita kada'i ko kuma ya sakar min jikata, sannan ya yi ta kansa nima na yi ta kaina.". Sai kuma ta kara fasa kuka, har da majina ta na kara fadin"Tsakaninmu da wannan yaron sai Allah ya isa." Lalle lamarin ya lalace tunda innani ke auna ma Sadiq Allah ya isa. Umma ta yi kokarin danne abunda ke ranta kai tsaye ta kalli Surayya kafin tace"meyasa tunda bai so mu sani ba ku ke sanar damu yanzu? Na dauka Tunda ya yi auransa a boye baya so mu sani ne, sai mu bar shi a haka tunda shi a wajensa haka ya zab'a." Surayya tace"Umma saboda matar ne, itama ya yi musu karyan ba shi da kowa  iyayensa duk sun rasu." Mama tace"Shi Sadiq din? Saddiqa tace"Shi fa, ai Sadiq ya bani mamaki ban taba Tunanin haka daga bangarensa ba." Mama tace"Ni kaina, ina ta mamakin wannan lamarin, abu kamar almara." Umma ta had'iye abunda ke ranta kafin tace"Ni banzan ce komai ba, ramar da yaso mu sani zai zo ya fad'a mana da bakinsa" Daga haka ta mike zata fita, Da Sauri Surayya tace"Umma kunsan matar fa." Da sauri Umma ta Juyo cikin mamaki kafin tace"Mun santa? Ta fad'a ta na kallon Mama, itama ta na kallonta. Cikin karin mamaki Mama tace"To wacece? Kafin Surayya ta yi mgana Saddiqa tace"Ina kawar saliha da tazo mata Biki daga zariya? Wace tace sun hadu da bikin salima a kaduna yar'uwan mijin salima wata Fara haka.". Umma da Mama suka yi shuru suna Tunani, nan da nan suka ganeta Tunda ai sun ganta. Saliha har falon Umma ta kaita suka gaisa, mama kuma a shashenta ta kwana ta gane, kuma kammninta ba shi da bacewa a fuska. ita Umma ma har a kaduna ta tuna ganin da ta yi mata Lokacin da ta fito neman Innani. Cikin mamaki Umma ta kalli Surayya kafin tace"Kuma kikace itama ya yi mata karyan ba shi da kowa? A ina ta san nan gidan? Surayya ta kalli Umma kafin tace"Umma koma ki zauna na yi miki wani karin bayani." Ba musu ta koma ta zauna, Innani ma ta daina kuka ta na saurara Abba dai ko a fuska bai nuna wani abu ba. Surayya ta warware ma Umma komai game da zuwanta Zariya..abu daya ta Boye na canfin da ke bibiyar Rayuwar Hasiya. Sai kuma na auranta Biyu, ta dai ce bazawara ce, Sadiq ya kama mata haya tana zaune a zariya ya na zuwa ya ganta in ya samu Lokaci. Sannan ta karishe da fadin"Umma ba wai ina so na kare Sadiq ba ne, A'a ina so ku fahimci namu ne mai laifi, itama ya yi mata karya ne ita da yan'uwanta, sannan dalilinsa na auranta wannan sai shi in yazo ya yi bayani, sannan mganar tasan nan gidan tamin Rantsuwa bata sani ba sai daga baya had'uwarta da Saliha a kaduna da kuma Hoton mu da tagani, tace sai da tazo nan ne taga komai, a yadda ta fad'amin ta na ma sadiq mganar ya kamata ya sanar da mu komai ammh sai yace ta bashi Lokaci yana so ya sanar daku ya na da wata matar kafin Sultana." Mama ta bude baki kafin tace"Bazawara? Shi Sadiq kamar wanda bakin uwa ke binsa? Innani ta ja hanci kafin tace"Magajin gida yaci Amana, kuma Amana sai taci sa ja'irin mayaudari kawai yazo ya sakarmin jikata domin bazata zauna da tsohuwar kilaki ba." Surayya da Sauri tace"Innani ba kilali ba ce fa." Innani na Hararanta tace"To wacece kuma ta yi aure ta fito ai ta zama kilali yar duniya, ina jikata zata iya zaman kishi da ita? Arhin dinsa sai ya saketa kuma naga abunda da zai hanani ci ma Saddiqu mutumci shi da wannan Dogon abokin nasa mai wuya kamar kauren langa Langa." Da Sauri Umma tace"Ba ruwan Tahir Innani, Abubakar ne bai Daukemu a bakin komai ba, nima ina goyon bayanki, yadda yaci Amanarmu shima sai Allah ya sa anci tasa, yata bazata zauna da shi ba, tunda wanchan ya zaba sai ya cigaba da zama da ita, Sadiq sai ya saki sultana tun kafin Mahaifinta yaji irin cin zarafin da ya yi ma yarinyar nan " Kawai sai ta fashe da kuka ta mike ta na fadin"Na yarda dashi, ban taba Tunanin zai karya wannan yardan ba,  Wlh tallahi sai dai ya zaba, ammh har acikin raina ban aminta da wannan auren ba." Ta na gama fad'in haka ta fice Abba na kiranta bata dawo ba, Innani ma ta tashi ta na dingisa sandarta ta shige dakinta itama ta na shan alwashin idonta idon magajin gida sai taci kwalarsa ya sakar mata jika bazata zauna da bazawarar kilakin matarsa ba. Abba ne kawai da Mama afalon, shi ta kallah kafin tace"Abban Siyama baka ce komai ba? Sai Abba ya dago kansa yana kallon Surayya kafin yace"Ki aika a dauko yarinyar nan shima Sadiq din ki gaya maasa yazo gida." Da haka shima ya tashi ya fice, bai bi bayan Innani ba sanim halinta tunda ta Dauki zafi bazata Sauraresa ba. Mama kuma sai ta gyara zama ta na kallonsu Surayya kafin tace"Ammh tsakami ga Allah Sadiq bai yi wayau ba, bazawara fa? Kodai farin fatarta ne yaja Ra'ayinsa? Daga Saddiqa har Surayya ba wacce ta kulata ta gama mganganunta itama ta tashi ta fita. Suma daga nab Shashen Umma suka koma ta shige dakinta ta Rufe, alamun bata son a dameta. Sai suka zauna anan falon suka yi shuru kowa da abunda ya ke sakawa. Saddiqa ta kalli surayya kafin tace"Sai ki kirasa ki fad'a masa ko? Surayya tace"Zan kira sa, ita Hasiya ina tunanin kawai zan ce ta hau motar haya in tazo tasha sai naje na Daukota." Saddiqa tace"Duk yadda dai ki ka yi, ni nafi son Sadiaq ya ci Ubansa hannun Umma da Abba saboda gaba" Surayya dai ba ta ce komai ba, ta na wani Tunani Abba bai nuna wani abu ba, Umma ce ta Dauki zafi ita da Innani kuma a irin kalamansu ba su karbi Hasiya ba. Kwata kwata su Surayya ba su dauka Mama zata gayama ya'yanta abunda ke faruwa ba, ashe ba haka ba ne ta na komawa daki ta fara kiransu a waya  daya bayan daya Sa'ima ta fara kira ta gayamata sannan Saliha da sauran. Kuma kowa sai ta yi masa kwatancen Hasiya sannan ta kara da fad'in ance ma bazawra ce, kuma Surayya da Sajida sun je har zariyan sun ganta. Dukkansu mamaki ya kamasu, Mama ko har da kalaman Umma da Innani sai da ta gayamusu sannan tace su zo gida ayi gabansu Tunda Abba yace a zo da yarinya sannan Sadiq ma yazo gida. Saliha tafi jin mamaki ta jima tana nanata abun, sai alokacin ta Tuna kiran da Surayya ta yi mata, ashe daman dalilin kenan? Salima ma Sa'ima ta ke gayamata, da kwatancen yar'uwansu mubarak yasa ta gane wacce Anty surayya ta Turo mata Hoton ta ne, ita ta manta da batun ammh jin haka yasa taji ta na son sanin komai. Ballatana da Mama ta kirata ta na fad'amata tace an ce yar'uwan mijinta ne, sai ta fad'a mata yadda suka yi da Big sis kwanaki. Nan ta ke Mama tace salima ta yi musu Binciken wacece Hasiya! Salima kuma na jin haka a daran ta matsa ma Mubarak sai da suka je gidansu, ta samu zahara'u ta tuna mata, itakuma sai da aka had'u wajen cin abinci ta ke yi ma Abba kwatancen Hasiya. Hajiya Murjanatu na wajen itace ma tace yar wajen marigayi dan'uwansa mamman ne. Sai ya tuna, kamar ko yasan Salima na son labarin duka nan ta ke ya fara ba su labarin Hasiya da canfinta na mai farar kafa da tunanin da suke yi ita tayi sanadiyar talauta mahaifinta daga karshe ya rasu da aure aurenta da komai sai da ya fad'a ma yaran kuma agaban Salima. Hajiya murjanatu na ta kifta masa ido ammh ya yi kamar bai gani ba. Da ya gama yaga ta na yi masa wani kallo sai kawai ya karkace kai kafin yace"To ko karya na fada? Gaskiya dayace fa daga kinta sai bata Murjanatu" Salima kuwa suma komawa gida ta kira Mama ta kwashe komai ta fad'a mata, ita kuma duk a daram ta kira yaranta ta fesa musu, suna ta faman Tattauna lamarin yan kusa sun ce gobe suna nan zuwa ayi komai a gabansu. Ita kuma Hasiya Surayya ta kirata tace in da kudi a hannunta ta shirya ta hayo motar haya in zata iya. Tace mata zata iya. A ranar na baro zariya na zo gusai, gwara kawai nazo ayi wacce za'ayi, a tasha Surayya ta zo ta Daukeni zuwa gidanta ta bani daki kuma ta karraamani. Ta kuma zaunar dani tamin bayanin komai da ya faru yau da safe, ammh bata fad'amin furucin Umma da Innani ba. Tadai ce Abba yace na zo sannan Sadiq ma a kirashi. Ta bar ni a dakin da ta saukeni ta fita falo da niyar kiran sadiq. Sai taga ya kirata ma wajen sau Hudu. Ta na kokarin bin bayan kiran ne sai ga shi ya sake kira. Sai da ta dauka suka gaisa, ta yi shuru shi kuma dagachan bangaran yace"Big sis mganar nan da na yi ta cewa ina so mu yi, shine yanzu na ke so in ba wani abu kike yi ba mu yi mganar" Kawai sai tace"ka makara Sadiq na riga nasan  mganar" Cikin firgici yace"Kin sani? Mirmishi ta yi kafin tace"Ba na kayi aure a zariya ba? Sunan matar taka Hasiya kuma ma yanzu ta na da ciki ko? Ai sai Sadiq yaji kamar a cikin kankara ya sandare a zaune. Yana kwaso in'inan mgana Surayya ta katseshi da fad'in"Umma da Abba da Mama hadda Innani suma sun sani, Sadiq gobe kome ka ke yi ka barshi ka taho gida, in kuma ka ki zuwa ina mai tabbatar maka komai zai lalace." Cikin rawan baki da na zuciya Sadiq yace"In sha Allahu zan taho da Sassafe.' Daga haka ta katse wayarta, ta na Tunanin abunda zai iya faruwa a goben. Abunda bata sani ba suna gama waya ya kira Hasiya, ta dauka kuma Daman Surraya tace kada na bari yasan ina Gusai. Cikin tashin hankali ya ke gayamin yadda suka yi da surayya sai naji ya bani Tausayi, barin ma da ya ke cewa"Gobe zan tafi gusai siya, ki tayani da addu'a Umma da Abba su Fahimceni, ina son ki har abada ba na fatan Rabuwa da ke. Ki zama cikin shiri akwai yuyuwar ki taho gusai in bukatar hakan ya taso." Ya yi ta kokarin ya nuna min kada na Damu in sha Allahu bakomai. Shi tunaninsa daya ina suka san da wannan labarin? Duk da na sani ammh na kasa iya gayamasa yadda abun ya fara ba. Muna waya ina sharan kwalla, na yi ma kaina alkwarin zan yi duk abunda Assadiq ya ke so, tunda wannan Halin Tsaka mai wuyar da ya ke ciki ba saboda kowa ya shiga ba sai saboda ni. *Janafty* *TMWBK3006* *TMW is a paid Novel, Pay 500 for regular or VIP N1K, Via 0552179550 Jamila Umar Gt bank, 09069067488* ‎Open this link to join my WhatsApp Group: https://chat.whatsapp.com/IhAz8h8nRy250ZnGGXwM65 Daren ya kasance mai tsawo a gareni, na kasa barci sai faman juye juye na ke yi, ga ciwon kai sannan ga cikina ya karamin nauyi. Domin na sha wahala a motar da na shigo zuwa gusau. Duk yadda Surayya ta rika lallashina da nacin na huta kada na damu babu abunda zai faru, sai naji na kasa jikina ya yi sanyi gabadaya gabbaina sun saki, in na kalli cikin jikina sai naji Rauni ya Rufeni, ba na so abunda muka aikata ya shafi d'an da ke Cikin mu, sannan gefe d'aya ina jin Matukar Tausayin Assadiq duk abunda ya faru ko zai faru saboda ni ce. Da naga na kasa barci sai na rarrafa na tashi ina jan kafa na fad'a Tiolet din dake cikin dakin na Dauro alwala nazo na daidaici in da Anty Surayya tace min gabas ne na tada salla. Dakyar na iya yin raka'a hud'u ina tsaye, da naji nagaji sai na koma na zauna saboda girman cikina kamar ana hurashi sai kuma ya koma kasan marata ya yi tulu kamar wacce ta shiga watan haihuwarta, alhalin kuma wattanin cikin wata bakwai ne. Na yi addu'a sosai acikin daran nan da Fatan duk abunda zai Faru gobe kada ya zama mai Tsauri ga Rayuwata sannan kada ya zama mai kuntata ga Assadiq. Sai wajen uku na dare na yi barci, kuma kiran sallar asuba a kunnina Tunda daren ne gabadaya ya yi min Tsawon da na kasa samun natsuwa ballatana na iya yin cikakken barci. Ko da Surayya ta shigo ta tasheni sai ta iskeni ina salla a zaune, tunda da asuba da jan kafa na iya shiga bayi, kafafuna daman tun jiya suka kara Kumbura saboda zaman mota, sannan ga sallar da na yi a zaune da safen sai suka kara hayewa dakyar na ke tafiya. Sai bayan na idar da sallah ta dawo mu ka gaisa cikin sakewa da Fara'arta kamar yadda na Fahimceta macece mai girmama Dan adam kamar irin Assadiq dina. Ganin yadda na mike kafafun ne yasa ta kalli kafafun sannan ta koma ta na kallon Farar Fuskata lokaci d'aya ta na fadin"Sannu naga kafar ta tasa ne" Mirmishi nayi ban yi mgana ba saboda jin nauyi sai itace ta cigaba da fadan"Allah yasa kada wannan yar mganan da za'ayi yau ya taso da naguda fa" Ta karishe fad'a cikin sigar Zolaya, sai na kalleta kafin nace"Ban kai ga watan haihuwata ba, cikina wata bakwai ne fa." Sai ta zaro ido ta na kara kallona kafin tace"Wata bakwai fa kikace Asiya.? Sai na gyad'a mata kai alamun hakane cikin mamaki tace"Ikon Allah gaskiya kina da girman ciki ni da Randami, ni wlh na dauka cikin ya shiga wata na Tara ne" Sai kawai na sunkuyar da kaina cikin Sanyin murya nace"Haka kowa ke tunani, ana ta mamakin girman cikina shiyasa nake jin nauyinsa a jikina da kafafuna." Cikin Tausayawa Surayya tace"Sannu dole zaki ji kam, bari na samo miki man zafi ki shafa. Ya samu su sauka kafin mu tafi chan gidan." Da Toh na amsa mata sai ta tashi ta fita ba jimawa sai gashi ta dawo ita da yaranta ta saka su, suka gaisheni na amsa ina tambayan sunayensu. Namijine ke ma uwar rad'a sai tayi dariya kafin ta kalleni ta na fad'in"Matar Uncle din ku ce Sadiq, sunanta Asiya." Sai ya waro ido kafin yace"Mommy ita Anty Sultanan fa? Batare da wata Damuwa ba tace"Dukkansu  matansa ne Khalil" Zai kara mgana ta dakatar dashi da cewa su je su yi shirin makaranta. Sai da suka fice ne sannan ta duka ta na fadin"Bari na taimaka miki." Ita ta shafemin kafafuna da man zafin nan, tace zuwa anjuma zai saki yadda bazai takurani ba. Ina tayi mata godiya kamar na yi kwallah ganin yadda ta karbeni batare da ta kyamaceni ba. Kafad'ata ta dafa cikin sigar lallashi ta na fad'in"Kada ki damu Asiya, ni a wajena da ke da Sultana duk d'aya ne Sadiq dai shine kanina duk da itama Sultanan kanwata ce, ammh a Ture wannan bangaran kuna da tudun matsayin matan kannena ne, kuma nice Babba a gidanmu in ban zama mai gyara ba, bazan so na zama mai barna ba kuma Dan adam ai ya na da Daraja bai kamata wani mutum ya kasance mai dariya ko wulakanta kaddaran wani wanda ba shi ya yi kansa ba." Har ta fice ina jin kalamanta a raina sannan a gefe d'aya ina kara jin na samu natsuwa a cikin raina. Kuma man zafin da ta shafamin naji dadinsa sosai, Assadiq ke raina shi na kira ammh sai wayarsa bata shiga ina da kyakyawan zato kila ya taso ya na kan hanya ne. Adda Fati na kira, a raina nace gwara na fara fad'a mata kada Lamarin ya Rikice na koma da wani Labari wanda su ba su san dashi ba. Da ta dauki wayata sai da tace min"Lafiya Hasiya? Saboda taga kiran wayata da Sassafe, cikin Boye yanayina nace"Lafiya lau Adda Fati ya yara? Ta amsa min Lokaci d'aya ta na tambayata ya nauyin jiki nace mata da Sauki sai tabini da addu'an Allah yasa na sauke lafiya acikin raina na amsa mata da Ameen. Shuru muka yi na wani Lokaci ita kuma sai ta Fahimci akwai mgana a bakina cikin Wani yanayi tace"Hasiya..! Menene ke faruwa ne? Cikin karfin hali nace"Adda ina gusau fa Tun jiya." Cikin mamaki Adda Fati Dagachan bangaren tace"Gusai kuma? Ta fad'a cikin Sigar Tambaya. Cikin gyad'a mata kai kamar ta na ganina nace"Eh Adda, ina Gusai yanzu haka ina gidan yayar Assadiq a nan na kwama ma" Cikin wani karin mamakin Adda Fati tace"Yayarsa kuma? Ke Hasiya yi min gwari gwari ni bangane ba." Sai na gyara zama na muskuta saboda na gaji da yadda na zauna. Cikin ajiyar zuciya nace"Labarin mai Tsawo ne Adda, ammh mafi muhimmanci ne shine Assadiq ba maraya ba ne, ya na da uwa da uba a raye sannan shi din d'an Dangi ne. A takaice dai iyayensa ba su san ya aureni ba sai yanzu da yayyensa mata suka gano hakan." Adda Fati baki ta Bud'e cikin mamaki da Al'ajabi kafin ta samu zarafin magana na katseta da fad'in"Na kiraki ne na fad'a miki Saboda ki sani, ba lalle na dawo da aurena a kaina ba, in komai ya rikice ba su aminta dani ba zan sake dawowa a sakakkiyar bazawara a karo na uku." Ban jira cewarta ba na kashe wayar Saboda kukan da ke neman kwacemim. Ina jinta ta na ta sake kira ban bi ta kanta ba, sai ma kaina da na kwantar saman gadon dakin na fashe da kuka, sai da na yi ma ishi sannan na share hawayena, na koma gefe ina sauke ajiyar zuciya. Acikin cikina nake jin motsin da yasa na Dafe cikin ina yar dariya, sai dai wani abu na bani mamaki ni fa ba Motsin abu daya na ke ji acikina ba, sanda naje awo na karshe na yi musu Complain suka kara yi min scanning suka kuma kara samun Tabbacin Rai d'aya ne aciki sai dai likitan yace ya Danganta da koshin lafiyan jaririn Cikina shiyasa na ke jin motsin kamar yafi rai d'aya. Ni dai na yi shuru ne, ammh har acikin raina nasan abunda ke cikina yafi guda d'aya saboda nauyin da na ke ji, sannan a tare zan ji suna Taushin Cikina ta bangarori da Dama, na yi dai shuru tunda wannan ne na Farko sannan kuma ban isa na san abunda Allah ya Boye a cikina ba, ko su likitocin ai sai abunda Allah ya ba su ikon sani suke iya sanin. Ina nan zaune sai ga Anty Surayya da Farantin kayan karyawa ta kawomin. Tace naci na koshi sai na yi wanka na Shirya in mijinta ya fita aiki zamu tafi chan gidan Cikin Sanyin jiki na amsa mata, alokacin bata ga idanuwana ba sai da ta dawo bayan na gama karyawa sannan ta lura da fuskata, cikin wani yanayi tace"Asiya ba nace ban da koken koken nan ba? Sai na dukar da kaina kafin nace"Ban yi kuka ba Anty surayya." Mirmishi ta yi kafin tace"Kin yi min karya , Saboda ai kinsan Fuskarki bata isa ta Boye kukan ki ba." Nan ta ke na gane kuskurena da sauri na bata hakuri sai ta kalleni kafin tace"Ni baki yi min laifi ba, saboda kinga halin da kike ciki, matsalane wani abu ya sameki a cikin wannan yanayin naki shiyasa kikaji ina ta miki mganar ki saka natsuwa a ranki in sha Allahu alheri ne zai Faru." Sai na jinjina mata kai, Tiolet ta shiga tace bari ta dauko Botiki Tankinsu ya lalace baya ba da ruwa sai an kira mai gyara. Da kanta taje ta juyomin ruwan da ta sanya a gas ya tafasa ta kawomin tace na gasa jikina da kyau, ban mata musu ba na tashi na cire kayana na Shiga wanka kuma kamar yadda tace na gasa jikina sosai kuma naji dadi. Da na fito man zafin nan da ta barmun na kara mulkema jikina Sai naji duk inda jikina ya Rike daga jiya zuwa yau ya sakeni. Doguwar rigar Abaya na saka mai Ruwan kasa, tunda kayan Atamfofi sun daina shigata saboda kiban da na kara da kuma cikin jikina. Nagama saka Rigar kenan ina Dauran gyalen kayan a kaina sai ga Anty Surayya ta shigo itama ta yi wankanta tas ta sha kwalliya sai tashin kamshi ta ke yi. Kafin ma nayi magana ita tafara washe min baki,ta na fadin"Kin gama Shiryawan Asiya? Da sauri na gyad'a mata kai alamun Eh, sai ta juya ta na fad'in"To dauko Hijabinki ki biyoni falo zaku gaisa da Dr ne." Ba musu na dauki hijabina dogo wanda ya kaimin har gwiwa fari na saka nabi bayanta zuwa falo, na iske ta zaune ita da Mijinta da alamu ma yana Shirin fita ne. Kaina na kasa na kariso tunda naji sanda tace"ka ganta dai Dr." Nayi kokarin na Durkusa sai na kasa na rike baya ina Cije baki da Sauri yace"Ke zauna kan kujera a bunki, ina ke ina Durkushe a wannan Halin da kike ciki." Jin haka yasa na zauna saman kujera kaina a kasa ina gaisheshi ya amsa Lokaci d'aya ya na kallona sannan ya na Bina da Sannu sannu. Surayya ya kallah kafin yace"Allah Sarki itama ai yarinyace kamar Sultanan nan." Surayya tace"Eh ko zata girmeta da kad'an ne, kila ta yi sa'ar salima." Sai ya jinjina kai kafin kuma ya murmusa yace"Abubakar Sulaiman Shinkafi i like u Staryle, ina son kanin nan naki Surry, Yana da wani irin Confident da Natsuwa tare da Hankali." Ta na kallonsa tace"Sadiq ne, Abba kan ce karamin su babbansu." Ya na yar dariya yace"Gaskiya ya fad'a  ko ni da na ninka shekarunsa bazan iya yin abunda ya yi ba, in kika Lura ko magana ki ke da shi farat daya zaki Fahimci ya na Tauhidi da kiyayewa Sabon Allah, ga shi he is so kind Mutum ne Simple Straighth Forward. Kai Tsaye zaka ga ya na yin abu ba shayi bakomai  ga Tausayi da zuciyar Taimako." Surayya na jin dadin kyakyawan Hallayar Sadiq da mijinta ke zayyanowa game da kaninta tace"Duk gidanmu ba kamarsa Sadiq na da kyakyawan zuciya." Dr yace"Sosai fa, kema wani Lokacin kuna kamanceceniyar Hali shiyasa taku tazo daya  sannan Namiji ne fa tsayayye, zai iya rike mata Hud'u kuma su zauna lafiya." Ya dago ya na kallona kafin yace"Ya sunan ki ne? Kaina na kasa nace"Hasiya!" Cikin mamaki ya kalli matarsa kafin ya yi mgana ta Rigasa da cewa"Asiya sunanta." Ina jinsu kamar zan ce ni ba Asiya sunana ba, sai kuma na fasa kada kuma na fara wuce iyakata. Cikin Yanayin maganarsa daga gani yana da barkwanci yace"Gaskiya kin yi sa'a Asiya, kin yi sa'ar samun Nagarttacen miji irin Sadiq." Sannan ya kalli Surayya kafin yace"Kudos to Sadiq, zan so mu had'u na sara ma Namiji Uban maza.". Hararansa ta yi kafin tace"Sai wani kod'asa ka ke yi ban gane ba ne? Yana yar dariya yace"Kina jinta ko Asiya? Kwantar da hankalin ki in zan kara aure ke zaki fara sani." Cikin gatsene tace"in ban sani ba ina ruwana Dr? Ba kaina zata zauna ba, ai ta mallam ba ta wuce Ameen" Dariya ya sska mata ya na fad'in"Eh kaji ta. Allah yasa to da gaske ki ke." Ya fad'a Lokaci daya ya na jan hancinta ba ita kadai ba har ni sai da na yi dariyan barkwancinsa. Ta make hannunsa ta na masa Hararan wasa mikewa ya yi ya na Fadin"Asiya na tafi, kada ki damu You are Welcome in to Shinkafi Family da yardan Allah." Kaina na kasa ban yi mgana ba sai dai na yi mirmishi nace"A dawo lafiya." Nan suka barni a falo Surayya ta tafi raka mijinta. Sai da sukaje haraban gidan bakin motarsa Sannan ya kalleta ya na fadin"Gaskiya Surry kada ki bari a wulakanta yarinyar nan, abar Tausayi ne da labarinta da kika bani, kuma ina da Tabbacin shima Sadiq Tausayinta yaji Shiyasa ya yi auran nan ba wanda ya sani." Surayya tace"Hakane ai da kanta ta fad'a tace taimakonta ya yi saboda mahaifiyarta." Dr yace"Nasan ta bangaren Abba game din mai sauki ne, Umma ce da Kakarku nasan sai kun yi ta ban baki da Nuniya." Surayya tace"Kamar ka sani domin tun ajiyan Umma tace bata yarda da wannan auren ba, ko ya saki Asiya ya zauna da Sultana ko kuma ya saki Sultana ya zauna da abunda ya zab'a, innani kuma kasanta Allah da su Allah ya isa jiya ta yi ta makama Magajin gidan nata." Dr ya jinjina kai yace"Daman ai za'a sha fama, ku dai ku tsaya mata don Allah, Umma ta Duba maraicinta tare da Rabon da ke tsakaninsu Thank god ma, sun yi aure da ta hanyar zina aka samu wannan cikin fa? Surayya tace"Nima tunanin da na fara yi kenan a farko naji Tsoron Allah ya kamani nace to yanzu inda ba su yi aure ba fa? karfin Rabon da ke Tsskaninsu yasa ya lalace." Cikin yar damuwa yace"To kin gani, ya kamata dai a duba lamarin cikin Fahimta sosai." Surayya ta tabbatar masa da cewa  in sha Allahu zata iya bakin kokarinta. Sun yi sallama ya shiga mota ta mika masa jakarsa ya karb'a ya na fadin"Yanzu Zaku tafi chan gidan ne? Sai ta girgiza kai kafin tace"Anya! Inaga sai anjuma kada mu je ta ga mutane ta kasa sakewa, kila sai Sadiq din ya iso." Daga haka Suka yi sallama ya tada Mota ta na daga masa hannu sai da megadi ya Bude masa get ya fita Ssnnan itama ta koma cikin gida, Direba ya tafi kai yara makaranta daganan zai kai motar gareji, tana Tunanin ita zata Tukasu ita da Asiya zuwa gida anjuma. Tana komawa falo ta ga Asiya har ta yi barci nan saman kujera. Sai ta kara jin Tausayinta a Fili ta Furta baiwar Allah yanzu haka jiya bata samu barci ba. Sai ta kyaleta ta koma dakinta ta Dauki wayarta sai ta ga Saddiqa ta kirata wajen sau uku bata kusa sai ta bi bayan kiran. Taji tsoro da taji saddiqa na gayamata labarin ya bazu a kunnen har wad'anda ke nesa, yanzu haka ma Shahida daga katsina ta na hanya, Salima ma an ce ta taho, Subai'atu ke fad'amata ta kirata da Safe tace zata zo gusai itama zata zo ne? Sai ta nuna mata a'a bazata samu zuwa ba  tunda sai adaran jiya ne Surayya ta kira Subai'atun ta na gayamata komai da kanta. Surayya ta rike baki kafin tace"To duk waye ya fad'a musu? Saddiqa dagachan bangaran tace"Kema kina da son jin magana wazai gayamusu wacce ta wuce mama" Surayya sai ta kasa mgana, Saboda Daman Mama irin matan nan ne da komai ya faru sai ta kira ya'yanta ta fad'a musu macece dai mai son hira da ya'yanta akan komai..abunda ba Halin Umma ba kenan wani abun ma sai an jima da yinsa su ke sani a bakin yan Dakin Maman. Saddiq ta katse mata Tunani da cewa"Saliha ce kawai kila bazata zo ba, ammh tun safe su Sakeena da Anty Sa'im suke gidan nan kuma nasan kan mganar ne." Surayya tace"Allah ya kyauta." Sai kuma ta kashe wayar saboda abun ne yazo mata a yadda batayi Tunani ba. Bata dauka mama zatayi haka ba, taso ayi komai cikin sirri a gama sai daga baya kowa sai yaji, Tunda dai kowa ya sani bata da zabi illah ta daga waya ta Kira Sadiya da Sajida da sa'adatu tare da Sajida tace su zo gida yau akwai taro. Dukkansu ba su yi mamakin kiran ba, a cire Sajida da tasan komai sauran sun ce su Sakeena ne suka kirasu suna fad'a musu abunda ke Faruwa suma kansu ya kulle daman suna Shirin zuwan gidan su ji in da kuma aka Haihu a Ragaya Tana mgana da Sadiya a waya ta na gani Saddiqa na kiranta ba ta yanke ba. Kuma suna gama mgana da Sadiya Subai na kiranta sai ta daga suna mgana ta na kara yi mata wasu bayanan ita kam sai fad'a ta ke yi ta na zagin Sadiq daman kuma ta na da fad'a Tun asali ita. Da surayya ta fad'a mata abunda Mama tayi sai kawai ta yi tsaki kafin tace"Allah ya kara masa uban wa yaja? Da bai aikata ba, wazai yi yawo da mganarsa. Kuma hukuncin Umma da Saddiqa ta fad'amin ya yi daidai sai dai ya zaba don Ubansa." Jin yadda ta Dauki zafi yasa Jikin Suryyya ya yi sanyi, ta so ayi wannan abu cikin Sirri ne bata Dauka abun zai kwabe haka ba. Bata kara sarewa ba sai da Subai ta tabbatar mata da ta na hanya itama zata zo, sai ta ci uban Sadiq kuma sai ta kara Zuga Umma saboda yasan abunda ya yi bai kyauta ba. Da farko Surayya bata damu ba ammh yanzu ta da fahimci gayya ne guda za su had'u masu bambamcin Ra'ayi sai taji tsoron abunda zai Biyo baya. Ita Asiya take Tausayawama ba Sadiq ba tasan shi Namiji ne kuma duk tsiya dai shi nasu ne. Falo ta lekoni sai ta iske har na gyara kwanciya sai barci na ke yi sai ta kyaleni ta shiga ciki ta na Tufka ta na faman warwara. Sadiq ta yi ta kira da farko wayarsa bata shiga sai daga baya ammh kuma baya Dauka. Sai kuma Hankalinta ya tashi ta Dauko ko wani abu ne ya same shi, sai da ya turo mata sakon ya na kan hanya ya kusa isowa gusau sannan ta samu natsuwa. ******* 11:13am Karfe sha d'aya na safe Sadiq ya iso Gusau motar haya ya shigo daga Abuja bai zo da Motarsa ba, saboda Halin Fargaban da ya ke ciki bazai iya Samun natsuwar tuki ba. Farko gidansa ya fara sauka Dake millions Quaters, ammh sai me Sultana bata nan, megadin gidan da Abba ya saka kuma ya ke biyansa albashi ya fad'a masa yace Tun safe suka fita da farko ya dauka Sun tafi makaranta ne. Ya na da key din gidan a hannunsa dashi ya yi amfani ya Bude gidan ya shiga ya ijiye kayansa ya yi wanka sannan Ya taho nan gidan. Yazo ya iske Abba baya nan ya fita Mallam Tajudeen ne ya ke fad'a masa Tun daga bakin get. Shashen Umma ya fara isa, nan ya Iske Saddiqa da Sadiya, a yanayin kallon da suke masa yasa ya san suma susan komai sai kawai ya had'e rai, ya na cin mgani hannayensa suna sarke cikin Aljihun saukakken Farin yadin da ke jikinsa dinki riga da wando na zamani. Umma na cikin daki, taki fitowa sai daya bita da kansa ammh kuma ya na durkusawa da niyar gaisheta yaga ta mike tsam ta bude kofar Tiolet ta shige da farko ya zata, ta shiga ta kama Ruwa ne zata fito sai da yaga yafi minti ashirin Umma bata fito ba ya zargi wani abu tunda shi dai bai ji karan Ruwa ba, kuma yaganta da wankanta tas ba wanka ta ke yi ba, in ya gane daidai shi ne bata son gani. Cikin wani yanayi ya fito daga Falon sai kuma ya had'e da Sajida da ta iso ba Dadewa sun had'a kai da juna suna ta kuskus. Suna ganinsa sai suka yi shuru suna kallonsu kallo daya ya yi musu ya Dauke kai zai fita, daman su Sadiya sun gaisa da shi da ya shigo, Sajida ce dai daman ba su gaisa ba. Har ya kama hanyar Fita Sajida tace"A'a Sadiq ba mgana ne abun? Kamar zai wuce sai ya fasa ya Juyo ya na kallonta kafin yace"Sorry ban lura da ke ba ne, Sajida ya gida da yaran? Bai jira amsawarta ba ya fice suka rakasa da kallon mamaki. Sajida ta rike Hab'a kafin tace"Wai yasan an san abunda ya aikata kuwa? Saddiqa tace"Oho masa, zuwa yanzu ai ina jin yasan karyansa ta kare, Big sis ta gayamasaa tunda Abba da kansa yace ta kirasa tace yazo." Sadiya tace"Ammh shi ko a fuskarsa ba alamun Tsoro ko nadama aciki.' Sajida tace"Nima ai abunda nagani kenan, uhm baku san Sadiq ba ne yanzu sai ya rufe bakin kowa da Ayoyin Allah tare da Hadisan manzon Allah, Salallahu alaihi wasallam. Sai Saddiqa da Sadiya suka yi dariya. Shi ko ya na fita sai ya rasa ina zai nufa, kawai sai ya tsaya nan kofar Bangaren Umma yana Tunanin ta ina mganar auransa da Hasiya ta bayyana? Duk iya hangensa bai hango masa wata kafar da ya bari a bud'e ba. Tun jiya ya yi Tunanin ko Tahir ne? Ammh da ya kira Tahir ya yi challaging dinsa ba su kara rabuwar dad'i ba ma wannan karon. Domin Tahir masifa ya faramai yana fadin da ya shiga tsaka mai wuyar da ya Sanya kansa aciki sai ya Kirasa ya na masa mganar Banza to ya saurara masa chan ya karata Tsuntsun da ya ja Ruwa shi ruwa zai yi ma dukan Tsiya kada ma ya kara kiransa daga karshe ya kashe masa waya. Daganan ya kara tabbacin ba Tahir bane  to waye? Ko dai Siya ce ta gayama Saliha? Ammh kuma ya na da kyakyawan yakini da Tabbacin Siya bazata yi abunda bashi cikin Tsarin sa ba. Yana nan tsaye ya na wannan Tunanin bai ji ko zuwan Siyama ba sai jin muryanta ya yi ta na gaisheshi. Cikin Firgigit ya dago ya na kallonta cikin mamakin ganinta. Bata jira amsawarta sa ba, Saboda sai taji tana jin Haushinsa sannan ta na taya kawarta Sultana kishi. wacce tun safe Umma ta kira su a waya tace sultana ta kwaso kayanta ta dawo gida. Sanda suka zo Umma sai taki cewa komai, Siyama ce ta je bangaran Mama ta na fad'a mata abunda ya faru sai Maman ce ke zayyane mata abunda ya Faru, nan take taji ta na jin Haushim Yaya Sadiq tunda yaci Amanar Sultana. Ita kuma Sultana har Anty Saddiqa kasa gayamata komai tayi, sai ta wuce bangaren Innani chan ne Innani ta zauna ta na kuka kamar an yi wani mugun abu ta warware ma Sultana komai har ta na cewa Hasiya tsohuwar kilaci ce Tunda an ce bazawarace ma ya aura ba yarinya ba, Ta yi tayi ma Sadiq Allah ya isa a gaban Sultana ta na kara fadin bata bashi har abada kuma bai isa ya yi ma Jikarta kishiya ba. Sultana bata san ya ake jin girman Kishi a cikin zuciya ba sai yau, kasa sarrafa kanta ta yi taji gabadaya zuciyarta na wani irin zafi, wani irin bala'in kishin Sadiq ta ke jin acikin Zuciyarta tare da jin Haushin yadda ya Wulakantata ya iya auran wata mace kafin ita, Sai ta fara kuka ita kuma Innani ba lallashi sai faman Zugata ta ke yi, ta na fadin ta yi hakuri Sadiq fa ko ya zaba ko kuma ya saketa kowa ya yi ta kansa. Ta na chan bangaren Innani ta na kuka, innani na gefe ta na kara iza Wuta, Farida ce kad'ai taje makaranta Allah yasa su sultana suna kokarin Fara jarabawar Fita ne. Sadiq ya bi siyama da kallo da ke neman Shigewa bangaren Umma. Cikin shakewar murya ya saka baki ya Kirata sai ta dawo ta Tsaya a gabansa. Cikin mamaki yace"Baki je makaranta ba ne!? Ina sultana? Kanta na kasa tace"Umma ta kira tace mu kawo kayanmu mu dawo gida." Ido ya zaro kafin yace"Ita Umman ta ce haka? Sai ta dago ta na kallonsa Lokaci daya ta na gyad'a masa kai. Cikin Fad'uwar gaba yace"To yanzu ina ita Sultanan? Kai Tsaye Siyama tace"Ta na bangaren Innani." Aransa ya Furta Tabdijam, yasan ai kuma komai ya lalace tunda ya na da tabbacin Innani ba ta tab'a gyara abu ba sai dai ta bata. Kai tsaye yace Siyama taje kawai shi kuma sai ya isa bangaren Mama su gaisa itama ya iske su Anty Sa'im,  Sakeena da salima wacce ta iso itama da wuri. Kamar na falon Umma suma daga gaisuwa ya hade ransa ya duka ya gaida Mama ta amsa ta na ta kallonsa cikin mamakin ganin ko razana bata gani a tare dashi ba. Daman kuma suna mganarshi ne ya Shigo sai suka yi shuru, suna ta maida yarda aka yi, Salima na kora musu wasu bayanan daga bakinta. Mama saboda maganar na cinta sai da tace"Sadiq sai kuma mukaji wani al'amarin na ban mamaki? Kai tsaye ya kallets kafin yace"Kamar na me fa? Sai Mama ta kasa mgana, ta koma ta na kallonsa shi kuma kawai ya mike ya yi mata sallama ya fita. Ya na fita Sakeena tace"Tabdijam yau akwai kallo a gidan nan" Salima tace"Ya Sadiq ya iya lauya jibesa kamar baisan abunda ya faru ba." Mama ta yi shuru saboda ta kasa mgana, Daman ita fa tasan Sadiq ba shi da Tsoro ba lalle su ga wani Razana a fuskarsa ba. Shi ko ya na fita sai ya rasa ina za shi, saboda a wannan Lokacin ya na jiran Hukuncin Abba ne, Umma kuma daman yaga ta riga ta dauki nata. Abu daya ya sani shine ya yi kuskuren yin aure ba da sanin iyayenshi ba. Ammh bai yi kuskure domin ya yi aure ba, sannan zai Tabbatar da cewa an yi masa Adalci kuma an yi ma Siya itama adalci. Yana Tsaye a haraban gidan, sai ga Subai'atu ta shigo gidan bayan mai adaidaitan da ta hawo daga tasha ya kawota da Sadiq ta fara cin karo ya na jingine jikin motar Abba. Tun daga nesa ta ke hararansa shi kuma sai ya yi kamar bai gani ba ya tareta ya shiga yi mata sannu da zuwa. Wani kallo ta yi masa kafin tace"Sai kuma idonka kenan Sadiq? Tare da bazawaarar matarka ta ka kake ko kai kad'ai kazo? Sai da yaji wani iri, ammh sai bai yi mgana ba, shi fa daman yasan irin wannan Ranar ta na zuwa sai dai Shirya mata ne bai yi ba. Sai kawai ya Daure Fuska kafin yace"Ni kadai nazo mana." Saboda bayan Surayya da Saddiqa ba wanda yasan Hasiya ta zo. Surayya tace kada Saddiqa ta yi zencen da kowa. Kai Tsaye ta kallesa kafin tace"Kai yanzu kana karamin yaronka da kai har kasan kayi mata Biyu? Kuma ka rasa waza ka aura sai bazawara Sauran wani katon? Kamar ya bata amsarta sai kuma ya fasa, yana jin zafin bazawarar da ta ke kiran Siya da shi sai dai shi yanzu fad'a ba nasa ba ne. Shiyasa ya na tsaye Subai ta gama gayamasa dukkan maganganun da ke bakinta ta kuma zageshi son ranta shi da Siya sannan ta wuce cikin gida Ransa ne yaji kawai ya fara baci, yana mamakin wai suna kyamatar Siya Saboda ita bawarawace  kenan susan komai da ya danganceta kenan. Turkashi lalle akwai kura. Gajiya ya yi da tsayuwa sai ya yi Tunanin ya tafi bangaren Abba, duk da shima kunya ya hanashi ya Kirasa. Yana kokarin juyawa yaji Hon a bakin get sai ya dakata. Mallam Tajudeen na Bude kofa yaga Motar Big sis, na shigowa gidan Saboda Hankalinsa na wajen Surayya bai kalli wacce ke gefenta ba ya Dauka cikin yan'uwansa ne dai. Ammh kuma ya sha mamaki bayan Surayya ta faka Motarta ta fito, ta dayan bangaren yaga wata ta fito mai kama da Siya dinsa. Kara waro ido ya yi sanda suka Doso sa, Hasiya na yin baya baya Surayya ta Rike mata hannu. Abun da ya kara bashi Tsoro shine Tabbss Hasiya ya ke gani, ammh kanta na kasa ta kasa kallonsa Tunda ta Fahimci shine. Na biyu kuma bakinsa na rawa yace "Siya." Ammh kamar ba su ganshi ba, ta gabansa Surayya ta wuce rike da Hannun Siya zuwa shashen Umma ko waiwaye. Bakinsa a bude har suka shige kafin ya Rufe zufa yaji na keto masa ta ko'ina, sai kawai ya samu kansa da maimaita Hasbullahi wani'imal wakeel. Ya kara Rikicewa ne sanda Motar Abba shima ta shigo gidan duk sai ya Daburce. Ya Dauka shima Abba zai yi kamar bai gansa ba ne, ammh ga mamakinsa yana ganinsa shi ya fara washe masa baki ya na fadin"Magajin gida ashe ka iso." Sadiq sai yaji kamar sai yanzu ne yake jin kara jin Guilty din abunda ya aikata. Rumgumesa Abba ya yi yana masa maraba da zuwa, sannan yaja Hannunsa zuwa bangarensa suna tafe ya na fadin"Ya wajen aikin naku? Fata dai ba wata matsala ko? Sai da Sadiq ya Hadiye miyau mai kauri kafin ya iya cewa"Alhamdulillah Abba." Daganan ya ja bakinsa ya Tsuke, sai dai ya na ta bin Abba da kallo domin ya Fahimci yanayinsa. Ammh ko a fuska bai ga wani alamun Sauyi tare da shi ba. Ajiyar zuciya ya saki a Boye a kallah dai ya samu yar salama Abba bai Dauki zafi dashi kamar Umma da Sauran yan'uwansa ba. *Janafty* *TMWBK3007* *TMW is a paid Novel, Pay 500 for regular or VIP N1K, Via 0552179550 Jamila Umar Gt bank, 09069067488* Haba Babyn Habiby ya zaki zauna kina ta fama cutar infection, ke ce rashin sha’awa, ke ce jin zafi yayin tarayya, ke xche d’aukewar ni’ima, ke ce kai’kayi ki fitar farin ruwa da sauransu, an yi maganin asibiti da na gargajiya amma duka dai, tau share hawayenki ‘karshen matsalarki ta zo, da Honeydrops infection flusher ko cleanser pro sai kin yi dariya da godiya don zai wanke miki duk wata cutar sanyi. Akwai original sabaya ta gyaran breast su cicciko kamar baki shayar ba, akwai ta hips da mazaunai ki yi ma sha Allah ki samu kaya kema su miki d’as ki bar yawo da doguwar riga. Na ce ba a nan muka tsaya ba muna da hadaddun kaya irinsu sweeteners, tighteners and wetners na tashin kan oga, wanda zai miki tukwicin dole, ke ko kurma ne sai ya yi magana ranar, don sumbatu ki dai samu abun rufe mai baki gudun ma’kota. Muna nan a garin Sokoto muna aike kowani gari kowacce kasa cikin aminci da rahusa. Kuna iya danna link din nan domin yi mana magana Kai tsaye https://Wa.me/2348167888934 ko kuma a kira 08167888934. Sai mun ji daga gareku isassun mata. Shi dai Sadiq yana zaune ne kawai a falon Abba, ammh kwata kwata baya cikin cikakkiyar natsuwarsa. Kunya tare da Nadama, da wani irin abu sun taru sun lullubesa da yasa ya kasa sakewa tare da Abba da ko a fuska bai nuna masa wani abu ba. Sai ma jansa da Hira kawai ya ke yi, bayan sun gama Hiran aikin sai ya koma masa Hiran abunda za'a fitar Saboda azumi ya gabato. Tun yana jin kunya har yazo ya sake ya na ba ma Abba amsa tare da shawarwarin da ya nema Daga bangarensa. Ganin da ya yi Abba ya shanye duka abunda ya aikata sai Kunya ta lullubesa da yasa ya kasa zama a kan kujera sai gashi durkushe gaban Abba a kasa cikin wani Raunin murya yace"Abba don Allah ka yafemin, nasan na yi muku laifi." Sai kuma ya kasa mgana ya koma ya sunkuyar da kansa kasa yana jin sai yanzu ne ma yaji meyasa ya aikata haka batare da ko sanin Abba ba? Abba kuma shuru ya yi masa na wani Lokaci kamar bazai yi mgana ba. Dalilin da yasa ya dago sai suka had'a ido da Abba da ya yi masa kuri da ido ya na kallonsa. Sadiq ya kara marairaicewa ya na fad'in"Don Allah Abba ka yafemin, ni har ga Allah da kyakyawan Niyar taimako na yi wannan auran. Kuma.." "Abubakar.." Abba ya katsesa bayan ya kira sunanshi, da Sauri ya amsa har bakinsa na rawa, Abba cikin muryansa yace"Ni baka yi min komai ba magajin gida, tun ranar da na san kayi wannan auran albarkata ke tare da auran naka, ni laifi d'aya ka yi min da ya fi min ciwo fiye da auran da ka yi." Abba ya karishe fad'a ya na kallon Sadiq da ke duke gaban Abba kamar zai yi masa sujjuda. Cikin mamaki ya dago ya na kallonsa kafin yace"Abba wani irin laifi ne wannan, wanda yafi boye muku auran da na yi girman Laifi? Mirmishi Abba ya yi kafin yace"Girman laifin shine har yau baka Fahimci irin girma da matsayin da ka ke dsshi acikin zuciyata ba Abubakar, girman yadda zaka iya yin abu mai girma haka batare da sanina ba, girman yadda ka ke tunanin ni bazan yi maka abunda ka ke so ba Matukar bai sab'a ma Shaari'a ba." Sadiq yaji kamar ya fashe da kuka ya na kallon Abba yace"Wlh Abba.." Abba sai ya dagamai Hannu kafin ya Cigaba da fad'in"Bacin raina d'aya da baka wareni cikin wad'anda za su zama Sirri kan sanin wannan al'amarin ba, Abubakar ko ba a zariya ba ko a birnin sin ne ka ga wata mace kana so batare da sanin kowa ba zan taka naje na nema maka auran ka, kuma nima zan iya sirrinta maka mganar har sai lokacin da ka so kowa ya sani, ai ni mahaifinka ne na fi kowa sanin kyakyawan hallayarka kuma ina da Tabbacin duk abunda zaka yi ko zaka aikatashi mai kyau ne" Sadiq cikin murya kamar zai fashe da kuka yace"Abba na yi Tunanin baza ku amince ba ne, tunda akwai mganar Sultana." Abba ya murmusa kafin yace"Ba wanda ya isa yaja da abunda Allah yace ayi, kai ai namiji ne kuma mijin mace Hud'u reras. Ba kuma wanda zai iya hanaka cike sunnar Ma'aiki Magajin gida, ni abu daya na ke so na muna maka shine ka yi kuskure ko a gaba ya kamata ka Fahimci ni nan zan iya tsaya maka a komai na Duniyan nan kuma na baka dukkan Goyan bayana sai dai in dan abun yafi karfina." Sadiq na sauke Numfashin Salama yace"In sha Allahu Abba, nagode sosai Allah ya kara girma." Abba ya amsa da Ameen Ameen ya na sake nuna masa kuskuran da ya aikata na Boye musu, tunda shi Lamariin aure ai ya wuce wasa. Sadiq ya kalli Abba kafin yace"Abba Umma ta Dauki zafi da lamarin, tace sultana ta kwaso kayanta ta dawo gida. Nima kuma da na zo yau ina gaisheta taki amsani daga karshe ma ta Boye ma ganina." Abba ya gyara zama kafin yace"Kada ka damu da wannan, bazan baka Shawaran ka rabu da daya saboda d'aya ba, duka matanka ne kuma zaka Cigaba da zama da su, na riga na yi mgana da Surayya nace ina bukatar son ganin ita iyalin naka ta Zariya Domin samun masalaha da Daidaito." Da Sauri Sadiq yace"Ai tazo Abba, na ganta tare da Anty Surayya dazu kafin ka dawo." Abba sai ya jinjina kai kafin yace"Shikenan ma hakan ya yi, komai zai warware in sha Allahu kada ka damu." Ya fad'a ya na Dafa kafad'an Sadiq din alamin lallashi, Sadiq sai ya yi Tunanin gwara ya fad'a ma Abba komai daya danganci auransa da Siya Tun yanzu kafin kuma daga baya yaji wata mgana  yar Sauran yardan da ke Tsakaninsu ta kara lalacewa. Nan ya zauna ya fara ba ma Abba Labarin Tun ranar farko da ya fara had'uwa da Hasiya har zuwa yau tare da Labarin duka auranta da kuma Kaddaran da ke cikin Rayuwarta. Abba ya ji matukar Tausayinta sosai shi kanshi a baya saboda Innani da irin manganunta ya na da dabi'ar rashin Tauhidi ammh godiya ga Allah da ya bashi yaro mai kaifin Basira irin Sadiq shine ya yi sanadiyar da yasa yasan Allah shine mai yin komai a lokacin da ya so, a kuma sadda ya so. Cikin Tausayin da ya bayyana har a saman Fuskarsa yace"Allahu Akbar kayi babban Jihadi Magajin gida, Allah Ubangiji yasa wannan abunda da ka aikata ya yi sanadiyar shigar ka Aljannah" Cikin Farinciki Sadiq ke amsawa da Ameen Ameen, Abba ya cigaba da fadin"Uwa ka share ma kukanta, kai ma watarana Allah ya baka ya'yan da zasu same maka sanyin idanuwana su kuma zamo masu jin kukan ka, sannan su kasance mssu share maka hawayen ka." Sadiq na ta amsawa da Ameen Sai Abba ya yi shuru ya na wani Tunani kafin yace"Mu bar wannan mganar a nan, kasan mata ba lalle su iya Fahimtar irin wad'anan abubuwan da Wuri ba. Kuma kaga innani yanzu ta na ji sai kuma ta Rikita al'amarin" Kamar Abba ya sani daman shi Sadiq ya fad'a ne saboda Tunaninsa ko har da wannan Labarin suka sani? Mganar Abba sai ta warware masa cewa ba su kai ga sanin haka ba. Abunda bai sani ba Shine komai da ya Danganci Hasiya bazai zama Sirri ba a yau. Suna nan falon Abba suna Hira Surayya ta kira Abba kan mganar gashi ta zo da Hasiya, sai Abba yace Sadiq ya fad'a masa ga su ma tarre. Yanzu an kusa kiran sallar azahar bayan sun je masallaci sun dawo su had'u a shashen Innani ta gaya ma su Umma. Daganan suka yanke Kiran, duk da Sadiq na jin tsoro sai dai yaji gwarin gwiwar samun Abba a kusa da shi, Daya tambayi Abba ko wani ne yazo musu da Labarin auran nasa? Abba yace Surayya ce da Saddiqa suka zo masa da mganar daganan ya yi shuru yasan Halin Big sis da bin Diddigi ya na da tabbacin har Zariya kila sai da taje. Daganan masallaci suka tafi suka yi sallar azahar, sun jima a masallacin Abba na ta gaisawa da Mutane makota abokan arzuka, Shi ya bata musu Lokaci suna hanya ma Surayya ta kira Abba sannan ta kira Sadiq. Sadiq ne ya amsa kiran nata sai tace masa suna shashen innani su kawai su ke jira, shiyasa suna shigowa gidan bangaren na Innani suka nufa kai Tsaye Abba na gaba Sadiq na bin bayansa kamar ya na kirga takun Abban. Da sallama Abba ya shiga Falon, Sadiq ya yi sallamansa iya a saman bakinsa ammh, Falon nan na Innani a cike ya ke da yan'uwansa mata shi ba su ne a gabansa ba Siya Idanuwansa ke son gani acikin falon. Bai lura da yadda gabadayansu suka Zuba masa ido ba, domin ya wani had'e rai  ya yi, yaso ma yazo da bakin glass din ya Rufe kwayar idanuwansa Sannan wacce ta masa shisshigi ko ta wuce gona da iri ya taka mata Burki, Ahto ai in sun girmesa ai ba su haifesa ba. Allah ya nuna masa Siya chan gefen Surayya ta Rakube baiwar Allah kanta na kasa, Tausayi ta bashi yasan a takure ta ke ko da ganin yadda ta ke ta mutsu mutsun zaman bai yi mata dadi ba, ko baka da juna Biyu kayi zaman tankwashe kafa na wani Lokaci ya ka ke ji, ballatana ga Ciki kuma ya Tsufa. Sanda ya biyo bayan Abba zuwa Cikin Falon, kamar zai wuce ta bangaran Siya da Surayya sai kuma yaga Umma gefenta Kuma Mama ce ta inda zai wuce irin kallon da Umma ta yi mssa ne yasa da Sauri yaje ya zauna a gefen kafafun Abba. Innani na zaune itama akan kujera kusa da Abba, ga sandarta a gefenta da gilashinta sai faman cin magani ta ke yi, Daga gefensa ne yaji ana ta jan majinan kuka da shessheka ya juya sai yaga sultana wajen kafafun Innani ta dunkule kanta ta na kuka. Mamaki ya kamasa miye abun kuka Fisabillahi in ba gata ne ya yi ma Mutum yawa ba? Karamin Tsaki yaja a ransa ya Kauda kansa, Innani kuma sai kallonsa ta ke yi ta cikin gilashinta ta na Hararansa, sai kuma ta waiga barayin da Hasiya ke zaune itama ta harareta. Gani tayi magajin gida ya kalleta ya watsar kamar yaga kashi yasa ta ture Sultana da rabin jikinta ke kusa da kafafunta ta na fadin"Ke ni ja chan sakara mara wayau? Miye kike wani kuka ni da nace miki ki kwantar da Hankalin ki, in dai ina Raye Magajin gida bai isa ya Tozarta ki ba, ke ba ma shi ba Kaf a falon nan ba wanda ya isa, ko da sulaimanun ne da kansa kuwa, Saboda haka ki bar kuka zan karb'an miki yancin ki, ba mai had'a ki zama da yar Bariki Tsohuwar kilaki." Ta karishe fad'a cikin Kufuluwa  Da Sauri Sadiq ya kalleta bai san bakinsa ya Kubce ba sai da yaji yace"Innani wacece Tsohuwar Kilakin? Innani ko ba tsoro da karfi ta nuna Hasiya da Sandar Hannunta Lokaci daya ta na fadin"Ga ta chan a wannan a bar mai kama da mayun da ka kawo  min cikin Zuru'ata mai Tsafta." Sadiq ya kara girman Idanuwansa ya na kallon Innani ransa na baci da karfi yace"Innani.." Bai sauke ma numfashi ba yaji Umma ta kira sunansa a fusace"Abubakar." Dole ya yi shuru ya koma ya na kallon Umma Lokaci d'aya ya na fadin"Na'am Umma." Cikin gargadi tace"Ka yi ma mutane shuru anan wajen Tunda baka da kunya." Innani na jin haka sai tayi kayci tace"Da kin barsa ya zageni, da yau kunga illar auran bariki ganin idon ku salamatu." Abba ne ya yi gyaran murya kafin yace Surayya ta Bude taro da addu'a a gefe daya kuma ya na mamakin ganin duka ya'yansa shi dai bai ce su zo ba, Sadiq kawai ya Bukaci gani da matarsa. Girgiza kai kawai ya yi, acikin ransa yace mata mata, duk abunda aka had'a da mata sai an yi Hakuri. Surayya ta yi sallama sannan ta Bude taro da addu'a. Kafin ta ce"Abba ga Hasiya matar da Sadiq ya aura kafin ya auri Sultana gata nan kusa dani." Ta fad'a ta na dafani, ni ko jikina ba inda baya rawa, daga fuskata kuma hawaye ne ke diga a saman Hijabin jikina na kasa dagowa duk da naji Idanuwam Assadiq a kaina ba maganganun Innani ne suka sakani kuka ba, Sai tun zuwana cikin gidan nan na Fahimci kaf cikin yan'uwan Assadiq ba wacce ke maraba dani sai Surayya. Tunda muka je falon Umma ita kad'ai ke kulani, na sha manganun cin zarafi a wajensu In Surayya ta taremun su taso mata, Umma kuma da ta fito Surayya tace na gaisheta bata amsa ba, Daga karshe ma tace duk su koma daki sai aka barni a falo kamar wata almajira. Daganan wasu suka shigo su Sakeena kenan yan dakin Mama suna kallona suna Tabe baki, na gaishe su suka amsa a wulakance kamar ba sa so, tun a lokacin jikina ya saki na ke kuma da Tabbacin ba lalle su bar dan'uwansu ya cigaba da aurena ba Ko yanzu da Innani ke ta aibatani bai Dameni ba, ni damuwata d'aya shine Assadiq ina cikin Tsaka mai wuya matukar suka ce zasu rabani da shi. Ina cikin wannan Tunanin naji Muryan Abba na fadin"Ma sha Allah, ta taso ta zo kusa da ni ta zauna itama." Sai gabadaya kowa a falon ya bi Abba da kallon Mamaki musamman ma Umma da Innani. Surayya kuma sai da ta Murmusa Sadiq kuma kamar ya goya Abba, Daman yasan Siya ta gaji da wannan zaman. Surayya ta taimakamin na mike Tsaye kafafuna sun haye sumtum, jikina na dan rawa ta kalleni kafin tace"Asiya ke ji Abba na kiran ki." Ba musu na gyad'a mata kai sanman na fara tafiya a hankali zuwa gaban Abba ammh na saka Hannu ina kare Cikin jikina duk da ban isa na Rufeshi ba Allah ya Riga ya bayyanar da shi. Ba gefen Sadiq na nufa ba sai nufa ta bangaran Damansa zan zauna sai naji Bayana ya kage, ina cije baki wajen na gyara kafata sai naji na Turgud'e kamar zan fadi. Kamar kiftawan Ido sai gani a Hannun Assadiq ya Rikoni cikin Sauri bakinsa na rawa yace"Siya ki kula fa.' Ya ke fad'a ya na kallona, Kaina na kasa ganin gabadaya falon ana kallonmu cikin Saurin na zame zan zauna da Sauri Assadiq ya kalli Abba ya na fad'in"Abba ka yi mata izini ta zauna saman kujera saboda lalurar da ke tare da ita." Da Sauri Abba yace"Ta zauna mana, ai ta na da uzuri, zauna zauna Bismillah" Abba ya ke fad'a da Sauri ko Sadiq ya zaunar da ni gefen Abba kunya ta kamani cikin sanyin muryata nace"Assadiq.." Shii..! Yace ya na kallona sannan ya Girgizamin kai, Dole na yi shuru sai da na zauna sannan ya duka ya mikar min da kafafuwana Lokaci daya ya na fadin"Ki bar su  a mike su d'an sake kinga sun kara kumburi." Ni dai kunya da wani irin nauyi sun hanani Dagowa, shi kuma ko ajikinsa sai ma tashi da ya yi ya koma bangaren Hagun Abba in da ya tashi ya zauna duk da yasan shi ake ta kallo ammh bai yarda ma ya Daga kai ba, ballatana ya kalli wani acikin su. Sultana ce suka had'a ido ta yi masa wani rin kallon, shi kuma sai ya kafeta da ido domin sai yaga kamar kallon yafi kama da na reni ya na so ya fahimci abunda ta ke nufi ne, sai kuma ya ga ta kauda kanta ta na sharan kwallah. Abba na zaune ya na d'an mirmishi Innani kuma sai ta hau kad'a kafa ta na Faman Tabe taben baki. Abba ya juya ya na kallona da naji duk na kasa sakewa cikin muryansa yace"y'ata ya sunan ki? Muryata na rawa nace"Ha. Hasiya." Sai Abba ya jinjina kai kafin yace"Sannu Hasiya, ina iyayen ki suke ne? Kai Tsaye nace"Babanmu ya rasu , sai mahaifiyata Amma ta na garinsu yanzu, sai yayyena guda Biyu da kanwata guda d'aya." Abba sai jinjina kai ya ke yi alamun gamsuwa kafin yace"Har na tsawon wani Lokacin kika san Abubakar? Assadiq na dago ina kallo sai naga ya Jinjinamin kai, shi ya bani karfin gwiwan yi masa bayanin Farkon had'uwata da Assadiq har zuwa auren mu." Abba yaji tabbas yadda Magajin gida ya bashi Labari ne, cikin gansuwa yace"Dakyau, shima haka ya fad'amin" Sai kuma ya yi shuru kowa ya zauna kawai ya na kallonsa mirmishi ya saki kafin yace"Na saka ma auran ku albarka, Allah ya sauke ki lafiya ina miki sannu da zuwa cikin Ahalina." Kowa sai da ya Bude baki ya na kallon Abba. Ni kuma shi na ke kallo idanuwana cike da kwallah nace"Ni? Sai ya gyad'a min kai kafin yace"Daga yau kema kin zama d'aya daga cikin Ahalina, gobe in sha Allahu zamu je Zariya gidan Baffanki da ya Daura muku aure na samu tabbaci." Sai kuma ya Juya ya na kallon Sadiq kafin yace"Ka kira abokin ka Tahir ya taho shima muje tare da shi." Cikin girmamawa Sadiq yace"To Abba , Allah ya kara girma." Kai Tsaye Abba ya kalli Sauran ya'yansa kafin yace"ga wata yar'uwa nan kun samu acikin ku, sai ku marabaceta cikin Ilimi kamar daman kun saba, ke kuma Sultana ki yi hakuri Bamu isa mu sauya wannan kaddaran ba, Magajin gida zai zauna da ku dukkan ku a matsayin matansa In sha Allahu." Umma ta mike a fusace kafin tace"Abban Siyama wannan wani irin Hukunci ne? Mama na gefe tace"Gaskiya fa, wannan ai ba mgana ba ce." Suma sauran nata kuskus, Surayya dai batace komai ba Sajida ne ke ta yi ma Sadiya rad'a suna Gulma. Sultana kuma kamar da kasa sai kwai ta fashe da kuka. Jin haka yasa kafin ma Abba ya samu Zarafin mgana Innani ta mike kad'an ma ya rage bata fad'i ba Saboda masifa tace"Ishunki Salamatu ai Sulaimanu bai isa ba, samman wannan Hukunci da ka yanke bai yi ba." Abba ya sauke Numfashi kafin yace"Innani wani Hukunci ki ke so na yanke bayan wannan? Innani na Huci tace"Ka yi masa fata fata na cin amanarmu da ya yi mana, bayan haka a gabamu ka saka ya saki kilakin nan a yi mata Korar kare shine hukuncin adalci Sulaimanu." Abba yace"Subhanallah Innani, Magajin gida aure ya yi ba zaman Haramci ba, kuma shi da Niyyar taimako ya yi wannan abun, mun zauna da shi ya yi min bayanin komai kuma ni na aminta da shi." Umma da ke tsaye tace"Kai ya yi ma bayani ai bai yi mana ba ko? Abba ya kalleta kafin yace"Hakane to ku koma ku zauna, kai Sadiq juya ka yi musu irin bayanin da ka yi min dazu" Sadiq da gabadaya yaji gwiwarsa ta sare, ni ya ke kallo ganin na dukar da kaina ina ta kuka komai fa zai Faru bazai bari a Tozartamai mata ba. Cikin gyara zama ya fara bayaninsa haduwarsa da Hasiya da auransu sai dai kamar yadda Abba ya Bukata ya Boye wasu abubuwan. Ya karishe da fadin"Kuma ni har Allah acikin zuciyata Tausayi ne, sai daga baya na Fahimci ba'a Tausayi in ba so, ina son Siya sannan Kuma ina son zama da ita har karshen Rayuwata Umma don Allah Ki Fahimceni." Umma cikin harzuka tace"In naki na Fahimceka fa? Nace in naki na Fahimceka fa? Sai aka yi ya ya? Kansa na kasa yace"Ki yi hakuri Umma, na yi kuskure kuma na yi miki alkwarin in sha Allahu hakan bazai kara Faruwa ba." Kai Tsaye Umma tace"Abubakar bazan karbi wannan auran naka ba, sannan kuma Wallahi Tallahi sai dai ka zab'a ko Auran da muka sani ko wanda ka yi ma kanka." Da sauri ya dago ya na kallon Umma kafin yace"Umma." Hannu ta daga masa kafin tace"Abunda nace shi na ke nufi, kuma anan wajen zaka zab'a, gwara Tun wuri nasan matsayin da ka ijiyeni." Sai kuma kawai ta Fashe da kuka, Innani ta yi zaraf tace"Kwarai mganar Salamatu haka take, gwara dai mu san matsayin mu." Abba zai yi mgana Innani ta daga sandarta ta na fadin"Ka na cewa Tak Sulaimanu kagani in ban kwad'a maka sandar nan ba." Duk da ana cikin Rudani ne, ammh bai hana wasu darawa ba. Abba sai ya koma kawai ya yi shuru ya na kallon ikon Allah. Sadiq ya rasa yadda zai yi ya tashi yaje gaban Umma ya duka ya na fadin"Umma don Allah ki janye kalamanki, duka ina son mata na kuma ina son zama da su bazan iya zabar d'aya na bar d'aya ba." Umma na sharan kwallah tace"Sai dai ka zab'a, tunda har ka iya nuna ko ni mahaifiyarka ba ni da ta cewa acikin Rayuwarka Abubakar" Yadda ta Juya masa Fuska ne yasa yasan ta riga ta yi fushi. Mama ya kallah tun kafin ya yi mgana tace"Sadiq gaskiya ne fa gwara dai ka sahale ma kanka, kafin ma ta san irin bakin fentin da ke tare da matar da ka aura." Ido ya kura mata ya na kallonta Umma ko da Sauri ta Juyo ta na fadin"Wani irin bakin fenti ne Suwaiba? Don Allah ki fad'amin." Mama ta Juya ta na kallon ya'yanta su Sa'ima su kuma suka gyad'a mata kai alamun ta fad'a. Surayya kuma Tsoro ya kamata sai ta kalli Sajida ita kuma sai ta ware mata ido alamun ni bansan komai ba. Mama ta gyara zama ta na fadin"kunsan dai salima na auran danginta, Alhaji jibril da ke kanin babanta da kansa ya ke fad'a ma Salima Matar da Sadiq ya aura Farar kafa gareta, duk wanda ta rab'u dashi ko asaran lafiya ko na dukiya ko na rai, Sannan da bakinsa ya fad'a yace tunda aka haifeta iyayenta ke ganin bala'i har sai da ta yi sanadiyar karayar arzikin Ubanta daga karshe tayi ajalinsa, sannan Mahaifiaryarta ta fara ciwom da aka kasa gane kansa, komai na su ya kare sannan kowa ma ya gujesu har su dangin Uban nasu, Sannan yace auranta Biyu na Farkon shima sai da komai nashi da na iyayen suka kare daga karshe ma zaman garin ne ya gagaresa, na Biyun kuma ranar Daurin aure ya samu had'ari ance har yanzu bai warke ba ya nakasa ga asaran dukiya, Wlh ance duk zuru'ar da ta shiga sai ta tarwatsasu sun rasa komai na su in ba'ayi asaran rai da lafiya ba fa an godema Allah." Gabadaya Falon sai ya Dauki salatin su Umma, Innani kam kamewa ta yi a zaune Tsabar tashin Hankali. Surayya kanta ta yi kasa da shi tasan komai ya lalace. Sajida kuma ta mata alama da Hannun cewa ba ita ta fad'a ba, sai yanzu ta tuna da Hoton da ta Turama Salima shi ya lalata komai. Kafin kace me salima ta karbi mganar ta na kara maida yarda akayi sai nanata take yi wai ance auranta ma Biyu duka ana sakinta Saboda bakin Jinin da ke tare da ita. Shahida ta saka salati Kafin tace"Sadiq yanzu wannan Annoban da kowa ke gudu kai ka kwaso mana? Sadiya kuma tabdijan kawai ta ke fad'i kafin tace"Wlh Umma Canfi gaskiya ne, mun shiga uku." Abba kuma na zaune yana jinsu, yana maimaita sunan Alhaji Jibril shi sai yanzu yasan Komai da mafarin lamarin. Yana ganin kimar Alhaji Jibril tun bayan da suka had'a auratayya a Tsakaninsu, ammh kuma wannan Labarin da yaji sai yaji kwata kwata ya raina masa ta ina zaka Biye ma wannan Abun da baka da Tabbaci a kansa? Kawai sai yaji kamar ya raina masa kwata kwata Tunda a baya yana ganinsa mai ilimi ne. Falon ya kaure da hayaniya  Umma kuka kawai ta ke yi ta na Hango kilama ta kusa rasa d'anta. Surayya bata da mgana Saboda su Shahida da Sadiya suna kara ma Umma Famfo kar ma Sajida ta ji labari. Sadiq sai kawai ya koma ya Dukar da kansa ya na kuma neman mafita ammh acikin ransa Hasbullahi ya ke ta maimaitawa. Ba wanda ya san lokacin da Innani ta tashi sai da akaji muryan Abba na fad'in"Subhanallahi  Innani lafiya? Sai aka juyo nan fa aka ga Inanni ta Daga sandarta zata makama Hasiya dake zaune ta na kuka. Fad'i ta ke yi"Ka bari na Rafketa Sulaimanu, wannan ai bakar dakace ta Shigo Cikin zuru'ata na bani ina jin ma ko mayyace zata lashe kurwan Magajin gida, namiji kwara d'aya kwal da Sulaimanu ya mallaka in wani abu ya sameshi ai mun lalace, ni Dije ina zan saka kaina, yau naga Bala'i ganin idona da maita." Ta ke fad'a ta na kuka ta na kokarin kwace sandar ta daga hannun Abba. A tare Surayya da Sadiq suka mike, sai dai ya Rigata isa kaina, tunda Innani ta saki sandarta da Hannu ta saka ta kaimin Dundu sai gadon bayan Assadiq Tunda ya yi min Rumfa. Bata ma Fahimci shi ta ke duka ba idanuwanta ya Rufe fad'i ta ke yi"Mayya Allah ya shiga tsakanin nagari da mugu, kurwan jikana Qur wlh, fita ki barmin gidana ki kuma Rabu da zuru'ata gabadaya." Ta ke fad'a ta na kuka, Sadiq ya Dago a fusace ya Rike Hannun Innani yana fadin"Kada ki kara kiran matata da Mayya. SIYA ba mayya bace itama Mutum ce kamar kowa." Ya fad'a cikin Tsawa kafin ya wancakar da Hannun Innani ya Dagoni jikinsa ya Rumgumeni kamkam, ni ko ina ta kuka ina fad'in"Assadiq don Allah kada ka rabu dani." Ya na rike dani yace"Babu wanda ya isa ya rabani da ke Siya." Sai jin muryan Umma ya yi ta na fadin"Har ni nan Abubakar.? Idanuwanta Jajir ya ke kallonta kafin ya mike ya rikoni nima na mike ya Rikemin hanmu gam gam. Sannan ya fara takawa dani har gaban Sultana  itama ya mika mata Hannunsa guda daya sai taki kamawa ta kauda kai ta na kuka. Da kansa ya Duka ya Riko hannunta itama ya mikaar da ita. Ya kuma Jimke hannunta acikin hannunsa na Hagu, muna gefe da gefensa cikin karfin gwiwa yace"Na karbi duka zab'in Umma, da zabin da kuka yi min da wanda Ubangiji ya yi min da siya, ni na aureta ba ita ta aureni ba Umma ki yi hakuri kada kice zaki Rabani da matana." Gadan gadan Umma kamar kabubuwa ta isa gabammu ta warce hannun Sultana ta na fadin"Ita wannan Annobar ka zaba kenan? Shuru ya yi ya kasa mgana Umma ta daka masa tsawa lokaci daya ta na fadin"Ka bani amsata mana." Kai Tsaye yace"Umma dukkansu ina son su, bazan iya barin d'aya saboda daya ba, ki yi hakuri." Umma sai taji kanta ma ya fara Juyawa, ta kure Sadiq da ido kawai ta na kallonsa ganin haka yasa na fashe da kuka ina fadin"Don Allah ki yi hakuri Umma" Ganin haka yasa Surayya ta rike Umma ta na fadin"Umma mu bi komai a sannu don Allah, mu godema Allah aure ya yi, in kuma ba auren ba ne fa! Zaki so ace Sadiq lalacewa ya rika yi achan? Ko kuma wannan Rabon fa ina za'a same shi? Ta fad'a ta na nuna cikin jikina, ni kuma sai kuka na ke yi ina kara Fadin"Ki yi hakuri Umma ammh don Allah kada ki saka Assadiq ya sakeni." Shahida ta katse ni da tsawa kafin tace"Dilla Rufema mutane baki Annoba kawai, ke har kina da bakin magana? Rabuwa kuma ai ya zama Dole sai dai kuma ki bi wani sarkin ba kanin mu ba." Sadiya ta karbe da cewa"Ahto muna zaman zaman mu kada tsiya ta Fara Bibiyan mu." Sajida tace"Kuma fa kuna ji fa bazawara auranta biyu, wannan ai bai yi ba kwata kwata." Sakeena ta Dorawa da cewa"To kuna dai ji su kansu dangin su sun gujesu Saboda ita, Sai shi zai rumgumota? Innani na gefe a had'a kai da Gwiwa sai kuka ta ke yi, ta na fadin sai an yi Turaren maita tunda ko na bar gidan Tunda na kwallafa rai sai na Bibiya kurwan jikanta. Abba ko na zaune bai yi mgana ba, so ya ke magajin gida ya tsaya ma matarsa da kansa, in ya yi hakan shi kuma sai ya tabbatar da nashi Hukuncin kamar yadda ya yi a Farko. Kowacce sai fadin albarkacin bakinta take yi a kaina suna aibatani da fadin dukkan kalaman da suka Fito daga bakinsu a kaina. Sun kirani da suna Annoba, da kuma mai bakin jini, mayya shi yafi Dagamin Hankali ba bazawaran da suke ta Jifana dashi ba. Sadiq ya gama jin iya abunda zai ji, yaga abun nasu ya yi yawa sai kawai ya kara Damke hannuna sannan ya Daka musu tsawa. Sai kowacce ta yi shuru suna kallonsu ya na faman zare ido. Hannunsa d'aya yasa ya na nuna su, Tunda Umma Surayya ta maidata saman kujera ta zauna ta na sharan kwallah. Sai da ya nuna su da hannunsa kowacce a saman Fuskarta sannan cikin Kaushin murya yace"Ya ishe ku, kun yi na kudin ku, kada wacce a cikin ku ta kara aibatamin mata Ya isa nace.!" Ya karishe fad'a a Fusace Subai'a ce ta taso masa ta na fadin"Bai isa ba, nace bai isa ba me zaka yi, Wlh kayi kad'an wannan Annobar ta zauna acikin mu" A fusace"Ina Ruwan ki? a kan ki zata zauna? Nace a kan ki zata zauna ko mijin ki ne zai rike min ita ballatana abun ya Dameki? Ya fad'a cikin kaushin murya, baki gabadayansu suka Bude suna kallonshi. Sa'ima tace"Sadiq ba dai rashin kunya zaka yi ma Anty subai ba? Idanuwansa sun kad'a saboda bacin rai ya sakar mata wani kallo kafin yace"in ma nayi mata ai ita taja, domin kun fara Tsallake abunda ba Hurumin ku ba, babu wacce zata gayamin yadda zan tafiyar da Rayuwata sannan acikin ku ban ga wacce na taba mata katsalanda a abunda ya shafi gidan auranta ba, Saboda haka kada na kara jin kun tsoma min baki, wannan mganace tsakanina da iyayena da abunda zuciya ta zaba ku fitar da kan ku aciki." Ya karishe fad'a cikin Tsawa har kuma Lokacin bai saki Hannuna ba. Sadiya ta saka salati kafin tace"Kai yanzu Sadiq akan wannan yarinyar mai kama da zubin mayu ka ke jayyayya damu? Wannan Shegen cikin na jikin nata  ko shi ka sani bazmu karb'esa ba." "SADIYAAA...! Sadiq ya wani Kira sunanta a Firgice cikin Tsawa da yasa har Umma sai da ta Dago ta na kallonsa. A fusace ya saki hannuna ya taka har gaban Sadiya ya daga hannunsa manuniya ya nunata da shi kafin yace"Kada ki kuskura ki ce zaki aibatamin mata sannan ki shegantamin gudan jinina, kada ki kuskura na gaya miki." Kawai sai tace"In ba haka ba fa? Ance shegen cikin, waya sani ma cikin ba naka bane Tunda tayi yawon dakuna sannan an san dadin zawar..' "Sadiya..!" Sadiq.." Alokacin da ya Kira sunanta ya Daga hannu zai kai mata mari, Surayya ta kira sunanshi itama a tsawace. Sai ya dakata lokaci d'aya yana Dunkule hannunsa sannan ya naushi iska. Cikin Tsabar Fushi da yadda Jijiyon kansa ke tashi Saboda bacin rai. Surayya cikin bacin rai tace"Ka bi a hankali mana wannan wani irin hauka ne, kai da ka ke kokarin gyara kuskurenka sai kuma ka bata shi da sake yin wani laifin? Ta fad'a cikin bayyana bacin ranta kafin ta kalli Sadiya ta na fadin"ke kuma Sadiya kin fara Tsallake iyakarki, in bazamu fad'i alheri ba sai mu yi shuru." Kawai sai Sadiya ta saka kuka ta na fadin"Mu ne yanzu Saboda mace Sadiq kana kanin bayanmu kana gaya mana magana, sannan har kana neman daga hannu ka maremu? Sa'ima ta karbe da cewa"Ko domin darajan mun girmesa ai ya raga mana." A fusace ya juya ya na kallonta kafin yace"Naji kun girmeni, ammh ai baku Haifeni ba sannan baku halliceni ba Allah ne ya Halliceni kuma shi kadai nake jin Tsoro kuma garesa kad'ai nake ninka bibbiyata, cikin ku ba wacce ta taba Daukan Ragamar Rayuwata, Saboda haka ku Rufemin bakin ku ku yi min shuru anan wajen." Cikin Kaushin Murya ya fad'a sai gashi sun yi shuru cikin sarkewar murya yace"Duk da ina karamin ku ina da girman da Ubangiji ya bani kaf din ku da Harkarina aka hallice ku, kuma iyayena Ubangiji bai ce na yi musu biyayya kan abunda nasan ya saba ma addina ba, kuma ina so na Fad'a muku wani abu game da Kaddaran Siya da kuke ta aibata ta akan haka to ku saurareni da kunnen basira ku ji wani abu." Ya dan dakata sai da ya kallesu d'aya bayan d'aya kafin ya fara fadin"Dukkan ku nan baku da iko a cikin kaddaran ku, kamar yadda itama Hasiya ba ta da wannan ikon a hannunta. In da ace Littafin kaddaramu a hannumu ake bamu mu zabi kalar Rayuwar da muke so mu yi a duniya na rantse da wanda raina ke Hannunsa cikin mu ba wanda zai yi kansa a yadda ya ke, kema bazaki saka kanki a wannan matsayin ba, nima haka to itama Hasiya haka bazata taba saka kaddaranta a haka ba, to ina so ku gane cewa Littafin Rayuwarmu da komai namu ubangiji ne ya ke Tsara mana komai, Hasiya ba Mayya bace sannan ita ba Annoba ce ba, duk abunda ya faru da ita ba ita bace ta yi silar Faruwarsu ba, Face Ubangiji da ya shiryama kowa kaddaransa sai dai ace itace Sanadi, kuma ku sani kuna wasa da Tauhidi sannan kuma hakan da kuka nuna ya kara tabbatar min da cewa baku san Qur'ani ba." Sai gabadaya suka fara kallonsa cikin mamakin kalamnsa. Kai Tsaye yace"Eh tabbas baku san menene Qur'ani ba, Domin duk wanda yasan abunda Qur'ani ya kunsa bazai yi irin manganganun da kuke yi ba, tunda munsan cewa kashi na Farko na alqur'ani Tauhidi tare da Bauta kashi na Biyu kuma al'amaru wannahi Umarni da Hani, kashi na uku kuma yana mgana ne kan Alkillas Labaran Annabawa da Al'ummar da suka gabata." Sai falon ya kara Daukan wani irin Shuru har da masu komawa ma su zauna, Abba na gefe ya na ta mirmishi hatta Innani da ke kuka sai da ta Dakata ta baza kunne tana Saurara. Ajiyar zuciya ya sauke kafin ya Cigaba da fadin"In da ace kunsan haka da duk baku fad'i mangaganun da kike fad'a a kanta ba, saboda haka ku sani Wani abu bai isa ya samu bawa ba face Abunda Ubangiji ya kaddara masa  ko ina tare da Siya ko ba na tare da ita Wani abu bai isa yasa na Gujema kaddaran da ke cikin Littafina ba. Sannan karya ne babu Canfi acikin Addinin mu, kuma kauce ma abunda Addnimmu bai zo da shi ba Farillah ne,hakan kad'ai ya isa ku gane cewa aurena da ita na cikin Littafin kaddarana." Ya sake yin shuru kafin ya kalli Sajida ya na fadin"Ke kuma da kike ta nanata ita bazawara ce? Miye illar bazawaran ko ita ba Mutum bace? Kada ki manta Annabi Rahma Sallallahu alaihi wasallam, ya auri Nana Khadija Ta na da shekara arba'in kuma a matsayin bazawara Annabin Rahma kuma na da shekara ashirin da Biyar, in da ace Haramcine da Annabi bai yi ba, ta nan ma ya kamata kusan zawara na cikin Tarihin musulunci, ke awa kice zaki aibata bazawara? Kina da tabbacin zaki Mutu a gidan mijin naki ne! Kina da tabbacin watarana bazai iya sakin ki ba ? Ko kina Tunanin watarana bazaki iya zama bazawara ba? Sajida ta zaro ido ta na kallon Sadiq cikin Subutar baki tace"Allah ya kyauta na zama bazawara." Kai Tsaye yace"Itama ai ba ita ta maida kanta ba  Allah ne, kuma kema ina kara Tusanar da ke cewa Kema Allah ne ya Halliceki kuma baki fi karfin kema Allah ya Jarabceki ba." Sai Sajida ta kasa mgana Tunda tasan gaskiya ya fad'a. Ni kaina na zauna na sunkuyar da kaina ina sauraran Assadiq ina sharan Hawaye acikin zuciyata na cika da alfaharin kasancewarsa Mijinta. Hannayensa duka ya zura a cikin Aljihun wandonsa kafin ya cigaba da fadin" Allah da kansa yace Annabi(SAW) man ikira'a suratul ilkasi, Suratul Iklasi salatalmanrat, Duk wanda ya karanta Qulhuwallahu har sau uku kamar ya karanta Qur'ani gabadaya ne. _Qulhuwallahu Ahad  Allah Ahad guda d'aya ne,  Allahu Samad Allah mai sama lam yalud walam yuulad bai haifa kuma ba'a haifesa ba walam yakun lahu kufuwan Ahad_ shine abun bukata kuma cikin Biyan Bukata._ _Walam yakun lahu kufuwan ahad kuma k bashi da kishiya acikin Bautarsa, Shi Ubangiji shi kada'i ne in kun yarda da shi da imani da duka Sahabbansa da littafansa zaku Fahimci abunda na ke nufi_ Gaban Umma yaje ya duka kafin yace"Umma ki yi hakuri ki yafemin, sannan ki karbi Ziya ki sakama auren mu albarka na yi miki alkwarin zan rike miki sultana da Amana kuma zam zama mai adalci a gare su." Umma dai kanta na kasa ta kasa mgana. Sai kawai ya mike Surayya ya kallah kafin yace"Big sis ki tafi da Siya gidan ki don Allah.' Harara ta makamai kafin tace"Ai da ya ke kai kazo da ita." Mirmishi ya yi bai yi mgana ba Abba ne ya mike sai da ya yi gyaran murya kafin yace"Ina nan akan matsayata, Ku karbeta da zuciyarku daya d'a na kowa ne sannan cikin mu ba wanda yafi karfin kaddara." Innani ta kallesa kafin tayi mgana Abba ya Duka gabanta ya na fadin"Ki yi Hakuri Innani ki saka ma magajin gida albarka, da ace ba aure ya yi ba akazo akace miki yana chan ya na lalacewa fa? Ko akawo miki yaro ace d'an gaba da Fatiha ne? Zaki so haka? Innani sai ta saka kuka ta na fadin"in sha Allahu haka bazai faru b Allah na Tuba ai gwara auren, ni fa daman Gayyar Tsiya ce ban so ammh tunda ya yi mana nasiha ni na saki sai dai Sulsana nake ji kada Ubanta yaji yace Saboda ba yarka bace shiyasa kayi shuru ammh tuni na saduda yar nan ki yafemin" Ta fad'a ta na jan majina, Abba ya mike ya na fadin"Kada ki damu kowa yaji yasan an yi abunda ya kamata, Abubakar muje a kawo mana abinci bangarena." Daga haka Abba da Sadiq suka Fice Surayya kuma ta zo ta kama hannuna muka mike ta na ce ma su Saddiqa su riko Umma zuwa bangarenta. Ni dai ina ta kuka muka fita Surayya na ta bani baki da lafiya komai fa ya wuce Abba ya saka albarka shi da Innani. Cikin kuka nace"Umma fa? Sai kawai tace"Itama zata sauko har ta saka musu albarka in sha Allahu" Saboda tasan halin yan'uwanta sai ta kira Sadiq yazo ya bata makulin Shashensa ta kaini chan tace na yi sallah za'a kawo abinci. Kuma da kanta tace min na saki jikina ina bangarem mijina ne' Na shiga Tiolet din bedroom na yo alwala na zo na daidaici gabas na yi sallah. Bayan na sallame na zauna na mike kafafuwana ina Tunani. Wayata ma achan gidan Surayya na barta, ajiyar zuciya na ke ta saukewa a kai akai, ta wani bangaren nasamu salama ta wani bangaren kuma ina cikin Tsaka mai wuya. *Janafty* *TMWB3K008* *TMW is a paid Novel, Pay 500 for regular or VIP N1K, Via 0552179550 Jamila Umar Gt bank, 09069067488* https://chat.whatsapp.com/I7uxPXgtPKBHnVQjaEbRlE *LAME NIG!* *KASAITATTUN MATA MUN GAISHE KU*. *AISHA LAME TA KAWO MUKU DUKKAN NAU'IN KAYAN KWALLIYA*. *KUNSAN GWANAACE WAJEN BAWA FATA HAKKIN TA* *KUN TUNA KYUAN FATAR GUDUYO KO?* *KUN TUNA DAI YADDA BULKACHUWA KE SIYAWA YABI KAYAN KWALLIYA NA ORIFLAME KO?* *TO KEMA GARZAYO KI ZABI NA KI, KO TA ZABA MIKI WANDA ZAI FI DACEWA DA FATARKI*. *BA IYA KAYAN ORIFLAME BA KAD'AI.* *TANA DA PRODUCTS DABAN DABAN MASU KYAU, MASU MASTAKAITAN FARASHI*. *KU TUNTUBE JIKAR DADAR MARINA A WANNAN LAMBAR 07036662633*. *ADO DA KAMSHI NE SIRRIN GAYU* Anty Surayya da kanta ta kawo min abinci tare da ruwa da lemu, farar shinkafa da miyar Naman rago. Kuma ta zauna tare da ni ta na lallashina har sai da naci abincin na sha ruwa ammh ina yi ina zubar hawaye saboda in na tuna kalaman Umma sai naji gabadaya na sare. Ta gama fahimtar abunda ke sani kuka shiyasa kafin ta fita ta dafa kafad'ata ta na fad'in"Asiya ki daina wannan kukan in ba so kike wannan Masifaffan mijin naki ya zo yaga kina kuka ya taso min ba." Idanuwana sun tara kwallah na kalleta ina Fad'in"Don Allah ki ba ma Umma hakuri kada ta rabani da Assadiq" Tausayina ya kama Surayya ta saka Hannunta ta na sharemin hawaye kafin tace"In sha Allahu zan iya bakin kokarina." Ko da bazata yi ba yadda ta nuna kula da Tausayina yasa na daina kuka sannan na tabbatar mata zan kwanta na Huta kafin mu tashi tafiya kamar yadda ta Bukata. Ficewa ta yi ta dauke da Farantin abincin da ta kawomin, ni kuma sai na Rarrafa na hau kujera na kwanta sai naji na kasa sakewa sai na tashi ina jan kafa na shiga cikin Bedroom Na sha kallo komai daman na Assadiq mai kyau ne da Tsari sannan duk da ya jima baya kwana a dakin akwai kamshin Turarensa sannan ga takalmansa nan da wasu kayan. Gefen gado na samu na d'an kwanta ta gefen cikina na Dama, da gasken kuma na gaji wlh sannnan ga kaina ya fara nauyi, bansan barci ma ya kwasheni ba ina chan ina Tunane Tunane makomar Rayuwar aurena da Assadiq. Cikin barci naji ni ajikin mutum sannan naji an zare min hijabin jikina, Hancina na kara Budewa ina shakam kamshin Turarensa, ina jin kamshin na ganesa, da Sauri na Bude idanuwa na sai ko fes acikin nasa ya na rankwafo ta kaina ya na kallona cikin Tattausan mirmishinsa. Cikin muryan barci na kira sunansa"Assadiq." Shima cikin wani sauti ya amsamin da cewa"Na'am Siya ta." Kawai sai na yi Ririmi na taso na fad'a jikinsa na Rumgumesa sai kuma na saka masa kuka ina fad'in"Assadiq bazan iya rayuwa babu kai ba, don Allah kada ka rabu dani zan zauna dakai na yi maka biyayya na yi ma yan'uwanka Biyayya sannan ka gayama Umma ni zan yi ma Sultana Biyayya wani abu bazai tab'a had'amu da ita ba, in dai har ni zan zauna dakai na amimce na yi komai Saboda kai Assadiq." Na karishe fad'a ina gunjin kuka shi kuma sai ya rumgumeni ta baya na. lokaci d'aya kuma ya na bubbuga bayana alamun lallashi. Bai hanani kukan ba sai da na yi ya isheni sannan ya dago ni ya saka Hannayensa tattausa ya sharemin hawaye Lokaci d'aya ya na fadin"Shii. Nace ki daina wannan kukan ko? Ko so kike wani abu ya samu Bbyn mu? Sai nayi shuru na koma na lafe a kirjinsa ina jan numfashi. Rumgumeni ya yi kam lokaci d'aya ya na sauke ajiyar kafin ya fara fad'in"Nace ki kwantar da hankalin ki matukar ina raye ni nan zan tsaya miki siya, ba wacce cikin yan'uwana da zan bari ta tozartamin ke zaki yi musu ladabi a matsayin su na yayyena ammh kuma ni ma bazan bari su wuce iyakarsu ba Mganar Umma kuma kada ki damu zata sauko in sha Allahu." Sai ya dakata kafin kuma ya gyara zamansa ya na dauke dani akan jikinsa sannan ya cigaba da fad'in"Sultana kuma ba ke ce zaki yi mata Biyayya ba itace zata baki girman ki, ko taki ko ta so ke ce na Fara aura kuma kina gaba da ita so a wajenta ya zama Dole ta girmamaki kamar yadda zata girmamani." Ina jinsa ammh na kasa mgana a raina ina fadin ai itace ke da kai ni ai yar karo ce. Fad'i ya ke yi"Zan kare ki da dukkan iyawata wajen ganin kin samu daraja acikin Ahalina fatana kawai ki yi hakuri ki gani, ki ki gani, ki ji kuma ki ki ji, kinsan gida in akwai mata da yawa sai a hankali balle ni kinga kanin mata ne sai a hankali ammh duk da haka zan yi kokarin na zame miki Garkuwa." Dago kaina na yi ina kallonsa kafin nace"Ka tabbata bazaka rabu da ni ba.? Na fad'a cikin Rauni, Shi kuma sai ya gyad'amin kai alamun hakane sai kawai na kara Rumgumesa ina fad'in"I love u." Shima cikin wani irin Shauki ya rikeni sosai lokaci d'aya ya na fadin"Love u too, and i miss u Siyan kuka i need u sosai." Ina jinsa ya fara shinshinar wuyana Tunda kuma ya Furta nasan abunda ya ke Bukata sai na dago kaina na kama wuyansa na rike, da kaina na Fara Sumbutar bakinsa. Kamar ya na jira shima ya Rike kaina ya na taikamamin wajen ba ma bakunan mu hakkinsu Mun shagala shagalar da ta saka muka manta da inda muke, Duk da nauyin cikina ban yarda na Juyama Assadiq baya ba, sai da komai ya wakana ina kwance a gefensa a tare muke maida numfashi. Tudun cikina ya shafa jin kamar Motsi yana mirmisshi yace"Shi kanshi ya na murna da zuwan Daddynsa." Mirmishi na yi ban yi mgana ba mun jima tare muna shakan numfashi juna kafin ya tashi shi ya fara shiga wanka ya Tsarkake jikinsa. Sai da ya fito nima ya taikamanin na yi nawa na fito na maida kayana, ammh shi sai da sauya wasu Tunda wad'ancan sun gama yamutsewa. Muna tare muna hira har wajen La'asar shine ma ya ke fad'amin zai fad'ama Abba gobe tare dani zasu wuce Zariya gwara na koma zan fi sakewa achan Tunda ga makaranta kada na yi wasa. Ban yi masa musu ba ni kaina gwara na tafin ko na ba ma wasu zuciyoyin daman samun Salama saboda zuwana. Kiran sallar la'asar yasa ya barni ya fita shima sai da ya taimakamin na yi alwala ya shimfid'amin Darduma ya zaunar dani yace tunda ya gajiyar dani na yi sallar a zaune sai nace masa kada ya damu zan iya. Allah ya taimaka ina idar da salla sai ga Anty Surayya ta shigo Cikin Shirin Fita ta na ganina na zaune tace"Au kin ma yi sallar kenan? To taso mu tafi gida sai gobe, tunda Abba yace tare da ke za su wuce." Ban mata musu ba na mike dakyar ina gyara Hijabina, da muka Fito Haraban gidan sai naga ta Nufi motar ta Cikin sanyi na nace"Bazamu shiga na yi ma Umma sallama ba ne?. Kai Tsaye tace"Muje gobe in zaku tafi kya shiga ki yi mata." Ban yi musu ba ta bude min gidan gaba na zauna sai dai ina ta waigen ganin Assadiq. Itace ta Lura da haka kai Tsaye tace min"Sadiq ya na bangaren Abba suna mgana, kina son ganinsa ne? Da sauri na girgiza mata kai ina kokarin kauda kaina Saboda kunya. Mirmishi ta yi kafin tace"Zai zo anjuma ina da tabbacin haka Tunda Siya na tare dani ta bakinsa" Tare muka yi dariya ni da ita , sai dai kuma Tundaganan har muka isa gida bata kara mgana ba. Abunda na Lura kamar ranta ya na bace ne shiyasa yara ma na mata Oyoyo mommy bata tsaya ta kansu ba, Tunda ta rakani daki tace na kwanta na kara Hutawa ta fice ta koma Dakinta. Ran surayya ya gama baci da sauran yan'uwanta marasa fahimta musamman Sadiya da Sajida da Subai, Saddiqa ce bata zafafa ba har Sa'adatu ta bata mamaki yadda taga ta Dauki zafin kan al'amarin.. Kuma illar shine daukan zafin su To kara Harzukan Umma suke ta so ne su taru su ba ma Umma baki ta karbi wannan kaddaran ammh su sun ki gane haka sai kara Zuga Umma su ke yi suna fad'in kada ta yarda Sadiq sai ya zab'a ko Sultana ko Mayyar matarsa. Kuma abun haushin harda karamar yarinya suka zauna suna ta zugata, ita sai ta koma kawai ta yi shuru Saboda sun ce ta na Goyon bayan Sadiq ne. Shiyasa da ta bi Umma har Daki zata ba ta shawara da mgana. Ta koreta tace ta fita ta bata waje har ta na cewa Daman tasan bakinsu d'aya da Sadiq abunda ya sa har ta yi kwallah shine sauran yan'uwan nata har suna zargin daman tasan Sadiq ya yi auren Tuntuni taki fad'a. Shine ya sakata kuka ta na Rantsuwa ta na bata san komai ba Saddiqa na tayata gayamusu in da taga Hoton Sadiq da matarsa. Kuma har Umma ta aminta da mganarsu Shiyasa ta zo ta ja Hasiya suka yi tafiyarsu. Kuma ita abunda yasa tace abi komai a sannu shine ta riga ta gama Fahimtar Matukar aka matsa to Sadiq zai zabi Hasiya ne ya bar Sultana domin alamominsa sun nuna haka, kuma wlh zai yi iya fad'a da kowa akan Hasiya to in suka zo suna zuga Sultana taje ta yi masa rashin kunya fa? Yadda Sadiq ya tsani Reni ai sai a samu matsala Shiyasa ta so abi komai a sannu a Hankali kowa sai ya samu abunda ya ke so. Ni bata gayamin ba ammh rashin walwalwarta ya bayyana har saman Fuskarta, tunda muka dawo ba ta da walwala ta ma shige ciki ba ta fito ba. Nima kuma ina inda na sauka na iske kiran waya Rututu har da na Amma ga na Ramatu sai na Adda Fati. Adda Fati kawai na kira, nasan itama ta na cikin Fargaban kawai sai nace mata ta bari na dawo gobe in sha Allahu. Amma na kira gabana na fad'i na Dauka ko sun yi wata mganar ne da Adda sai naji kawsi mun gaisa ta na tambayan lafiya da kuma lafiyar Assadiq nace mata dukkan mu muna cikin koshin lafiya. Shine ma ta ke fad'amin Adda bata ji dadi ba hawan jini ya taso mata kwanaki biyu kenan, sai nace ta bani ita na gaisheta. Adda da karfin hali ta tambayeni Cikina watansa nawa? Nace bakwai da wani abu sai tace In Hamma Isuhu zai Shigo Zariya zata bashi wasu saiwowin itattace na Dafa na rika sha mganin zaki ne, ni dai sai na bita da Toh kawai. Bayan Amma Ramatu na kira muka gaisa itama mun kwana Bamu yi waya ba tambayata tayi ina gida gobe sai nace mata a'a sai dai jibi, nan take gayamin Jibi zata shigo da haka muka yi sallama. Da daddare Khalil ya kawo min abinci Tuwon Semo miyar Kubewa d'anya, kuma naji dadi Sosai naci da yawa Sannan ga Zobo mai sanyi ga dad'i. Bayan na gama ci ne na yi sallar Isha'i daman kuma sai da na yi mangariba na ci abinci bayan na idar da salla ina zaune naji tashin murya kamar ta Assadiq a falo kuma chan sai naji kamar harda muryan mijin Anty Surayya. Ban ko kai da tashi daga inda na ke ba sai gashi ya shigo. Ina ganinsa na sakar masa mirmishin jin dadin ganinsa. Shima sai ya maidamin martanin mirmishi kusa dani ya zauna Lokaci Daya ya na kallon kwanukan gabana kafin yace"Lalle kin zama yar gata a wajen Big sis." Mirmishi na yi kafin nace"Ai ta na da Kirki ne." Kai Tsaye yace"Shiyasa na fi sonta duk cikin su, ita da mijinta suna da kirki yanzu ma afalo da ita nake yi, Matar nan fa wai batamin magana yanzu Saboda taga agaban mijinta ne har da kukanta wai naja mata zargi a wajen Umma da Sauran yan'uwana." Ido na zaro kafin nace"Zargin me kuma? Yana Mirmishi yace"Zargin suna Tunanin Ta san nayi aure ammh ta Boye musu." Jinjina kai na yi kafin nayi magana ya Rigani da fad'in"Sun ce hakane Saboda susan ba abunda na ke Boye mata  abunda ba su sani ba itama yadda suka ji haka itama taji sa.' Kai na lamgwabar kafin nace"Ai kai ne baka kyauta ba" Mirmishi ya yi kafin yace"Nasan ban kyauta ai na karb'i Laifina ko? To ba sai a Tsaya a saurareni ba." Ni dai ban ce komai ba, sai naji ya Rungumoni ta gefen kafad'ansa Lokaci d'aya ya na fadin"Matar Sadiq ya nauyin jiki kuma? Dariya na yi ina dukan kirjinsa nace"Nauyin jiki ko Nauyin ka? Gira ya dagamin kafin yace"Duka na ke mgana." Dariya muka saka gabadaya ni da shi, ina gefen kafad'ansa ya dafani kamar wata kawarsa ya na min Hira shiyasa na ke son Assadiq saboda Halinsa na kwarai da sanin yakamata. Acikin Hirar ne ya ke gayamin Abba yace da wuri zamu dauki hanya. Ina kallonsa nace"abokin naka fa, ka kirasa ne ?. Kai tsaye yace"Tahir ai ba shi da kirki gaba ya ke yi dani, na yi ta kiransa bai Dauki wayata ba sai na Tura masa sako in yagani shikenan in bai gani ba Shiya sani." A marairaice nace"Duk Saboda ni ne ko? Ni dai don Allah kada ka bata da abokinka saboda ni." Da Sauri yace"No kada ma ki saka wannan Tunanin a ranki, ni da Tahir mun saba kada ma ki yi wannan Tunanin." Ya fad'a daidai Lokacin da wayarsa dake gaban Aljihunsa ta fara Daukan Tsuwwa. Ni na saka Hannu na Dauko masa wayar na mika masa, ya na Dubawa sai yaga Tahir ne. Ni ya kallah cikin mirmishi kafin yace"Kinga Mutumin ki ko? Tahir ne" Yana fad'a ya na daga wayar kamar Tahir na jira yace a kufuluce"Mallam wani irin sako naga ka Turomin? Sadiq na jin haka sai ya saka wayar a Speaker ya na Danne Dariyansa. Shima cikin kai Tsaye yace"Ka karanta mana, ai da Hausa na yi maka Sakon." Shuru Tahir ya yi kafin yace"Naga wai kace Abba na nemana zamu je Zariya, Mallam baka ji abunda na fada maka Tun Farko ba ne? Ni ba ni cikin wannan Rigimar taka, tunda tun Farko kasan bazan barka ka aikata haka ba shiyasa ka Boyemin Saboda haka Count me out acikin Rigimar ka na gayamaka." Da Sauri Sadiq yace"Haka zan gayama Abban? Tahir yace"Bangane ba" Sadiq na danne dariyansa yace"Abba ne yace na kira ka na fad'a maka zamu je Zariya gidan Baffan Siya." Tahir yace"Saboda mene? Meyasa sai da ni kuma? Kai Tsaye Sadiq yace"Saboda kai ne waliyina." Tahir ya yi shuru bai yi mgana ba, Sadiq yace"Me zan gayamasa? Bazaka je ba? Tahir yace'"Ban ce ba, d'an sharri sai dai mu Had'u a zariya tunda baka gayamin da wuri ba." Sadiq yace"Better.." Daga haka suka yanke kiran ya kalleni ya na fadin"Kin jisa ko? Tahir ai dan renin sense ne." Mirmishi na yi sai dai ban yi mgana ba, hira ya cigaba da min yana bani Labarin Diramansu da Tahir ina ta Dariya. Bamu san lokaci ya ja haka ba sai da Mukaji muryan Surayya daga sama kanmu, cikin cogewa a bakin kofar dakin tace"Mallam kazo ka tafi zamu Rufe gidanmu ne". Ta fad'a lokaci d'aya ta na hararansa, dukkanmu muka kallesa ni kuma kunya ce ta kamani,ina ta noke jikina ganin Assadiq yaki sakina. Shi ko Surayya ya kallah kafin yace"To tunda zaku Rufe gida ko na kwana anan ne? Ya fad'a ya na kallonta ita ko sai Faman balla masa harara ta ke yi, yar dariya ya yi kafin ya cigaba da fad'in"Tunda daman gobe zamu yi tafiya daganan sai mu wuce kawai." Ko mgana batayi masa ba, sai shigowa dakin da ta yi, ni ko ina ta son kwace jikina ammh yaki sakina. Surayya na zuwa ta duka ta Masa katon Dundu a gadon baya kafin tace"Tashi ka fita kafin na sab'a maka wlh" Bayansa ya sosa Lokaci d'aya ya na fadin" Big sis." Kara Dukansa ta yi, ganin haka sai ya bi ni ya kamkameni ya na dariya ni kuma sai na ke fad'in"Anty Surayya ki ce ya sakeni." Surayya ta Rarumo Filo ta daga sama ta nuna Assadiq ta na fad'in"Sakarta ko yanzu na yi maka Rufdugu a saman kan ka." Ganin yaki sakina yasa ta fara makamasa Filo ta na fadin ya sakeni sai da yaga dama ya Cikani ta kuma ja hannunsa ta fitar da shi daga dakin ina gani yana Dafa kafadarta ita kuma tana Turesa. Sai naji sun Burgeni daga gani suna da kyakyawan Fahimta a tsakaninsu. Ina ta jin hirarasu har na yi barci bansan Lokacin Tafiyar Assadiq ba. Washegari tun Asuba Anty Surayya ta sakani na yi wanka na Shirya cikin Abaya na Maryam's Eyptian Abaya Tunda yanzu ne kayan sawa na. Ko kafin takwas na safe na karya na sha Tea sannan na ci soyayyan Buredi. Tunda tace Sadiq yace ta kaini chan gida da wuri  tare muka fita da Mijinta ya kaimu ya sauke sannan ya wuce wajen aiki. shima yana ta bani baki da nuna min na kwantar da Hankali ba wata matsala. 20k ya bani bayan Anty Surayya ta bani Ruguna bubu da yawa, ga kuma kayan kwalliya har da kayan jarirai Sabbi Overroll, ta kuma Tambayeni ko mun fara siyan kayan Haihuwa? Sai nace mata a'a, nan take tace zata yi ma Sadiq mganar ya kamata mu fara siya tunda Haihuwan ta kusa Bangarem Umma muka fara sauka, Sabai ne da Saddiqa su Sadiya sun koma gidajensu tun jiya da Daddare. Na duka har kasa na gaishe su Anty Saddiqa ce kad'ai ta amsa banda Anty Suba'atu. Umma kuma har ciki Anty Surayya ta shigar dani na gaisheta, kallona ta yi kawai ta kauda kai bata amsa ba sai ma ta tashi ta shige Tiolet ta barmu nan zaune. Anty Surayya bata damu ba ta Jani har bangaran Mama, in da su Salima duk suna nan suma dai kalilansu ne suka amsamin cikin sakewa kasa kasa suna karemin kallo. Mama ce ta amsa cikin sakewar har tana ce min ya bakunta? Kaina na kasa nace lafiya. Muna zaune Shahida ta kalli Surayya kafin tace"Ki ce gidanki ta ke da masauki kenan? Surayya ta kalleta kafin tace"Ai ba ma ita ba, ni kinsan gidana masaukin baki ne, ballatana ita Asiya ai ba bakuwa bace yar gida ce Tunda matar Sadiq ne." Sai gabadayansu suka wani tabe baki, mama da Sauri tace"Umma ta hakuran kenan? Kai Tsaye surayya tace"Umma ai bata isa ta ja da abunda Allah ya tsara ba, ko bata Hakura ba, ba wanda ya isa ya tada wannan kaddaran na auran Sadiq da Asiya" Duk sai ta kashe bakinsu, daga haka ta yi musu sallama muka fita bayan Salima ta tambayi Surayya tare dani za'a je zariyan? Tace musu Eh. Daganan sai bangaren Innani chan mukaje muka tarar da Sultana da Siyama. Har gaban Innani Surayya ta kaini na gaisheta ta amsa ta na kallon Surayya kafin tace"Ita wannan fa? Ta fad'a a gatsine Surayya tace"Matar magajin gida ce Asiya." Da Sauri innani ta washe baki kafin tace"Allah Sarki sannu yar nan, ki yi hakuri da abunda ya faru jiya duk sharrin shed'an ne, mu bamu ki karban ki ba ne, Daman saboda marainiyar nan ne Sulsana ba ta da kowa sai mu, kuma ni daman ban ja ba ina Ruwana da shiga Hurumin Allah. Ni dai yar nan rokona gareki ki rike magajin gida Amana kina dai gani bayan shi Sulaimanu ba shi da wani magaji sai shi, in ya rasashi bansan wani hali zai shiga ba, ni dai fatana kada wani abu ya samu magajin gida shine kawai damuwata." Sai kuma ta saka kuka ta na wani gyara gilashinta kafin tayi kyafci ta na jan hanci tace"Ashe da rabon zan ga kwan magajin gida ina Raye? Allahu akbar yar nan Allah ya rabaku lafiya.' Ta ke fad'a ta na jan majina, Surayya na gefe ta na mirmishi. Sultana da tun shigowarmu ta maida kanta ta sunkuyar sai da ta dago ta na kallon Innani lalle ka tsoraci Duniya ka Tsaraci Innani, yanzu nan fa zagin Hasiyar ta gama yi ta na fadin sai magajin gida ya saketa ammh shine har ta sauya mgana. Ni dai kaina na kasa, Innani ta na ta addu'a ina amsawa da Amin sai da wayar Surayya tayi kara ta fita waje sai gashi ta dawo ta na cemin na tashi mu tafi Sadiq yace sun shirya. sallama na yi ma Innani ta amsa ta na Fad'in "Yanzu chan Zariya zaku tafi? Sai na amsa mata da Eh da sauri tace"To Allah ya tsare haka sulaimanu yace min da ya shigo da safe ya gaisheni, Sulaimanu bawan Allah nan ya zauna yana ta min nasiha, tuni ni na Saduda daman Saboda Sulsana ce in naga ta na kukan nan duk sai na Rude na rasa bayan wa zan bi." Sai kuma ta yi shuru kafin tace"Ni fa an sakani a Tsakiya magajin gida ma fushi ya ke yi dani Tun jiya ko shashen nan bai kara kallo ba, oh ni Dije in nabi bayan Sulsana ace na yi son kai, in nabi bayan wannan yar Farar sai ace na so bare naki nawa." Ta ke fad'a kamar gaske ni kaina sai da ta bani Dariya. Surayya tace"Bakomai Innani in kika so nakin kika had'a da baren kika so gabadaya baki yi laifi ba." Da haka ta kashe bakin Innani muka fita tana mana fatan Allah ya kaimu lafiya. Har ta na fadin"Yar nan sai yaushe? Na kasa bata amsa Anty Surayya tace"Sai tazo gabanki, ai ke zaki karbi zuwan d'an magajin gida." Innani sai kuka,ta na fadin Allah yasa tana raye zata gani har muka fita bata daina kuka ba. Muna fita Siyama ta kalli Innani kafin ta yi mgana Sultana ta mike fuu ta shige uwar dakin Innani. Daga innani har Siyama suka bi ta da kallo, Innani ta tce"Ita kuma wannan me aka yi mata? Siyama tace"Ba ke bace, yanzu kina nuna kina goyon bayan mu, ammh kuma yanzu kina ganinta kika wani ware mana baya." Innani ta saki baki kafin ta yi mgana Siyamar ta mike tabi bayan sultana su bacin ransu Yaya Sadiq baisan ma yazo ya Lallashi Sultanan ba. Innani ta bi su da kallo kafin ta tabe baki tace"Kaji min tsiya, yaran da ba su san abun arziki ba, na yi mgana Sulaimani da magajin gida sun ce ina ja da Ubangiji ai dole nayi shuru da bakina." ******** Mun dauki hanya wajen goma saura na safe, Kamar kada mu rabu da Anty Surayya saboda kirkinta Abba ma ba ruwansa kafin ma na gaishesa shi ya fara gaisheni. Sadiq ke tukin Abba na gidan gaba ni kuma ina baya, suna tafe sai hiran su suke yi gwanin sha'awa. Abba ne ke juyawa yana sakoni a Hirar shi kuma Assadiq bini bini sai ya Waiwayoni yana tambayata ya ya? Saboda yaga ina ta mutsu mutsun Tunda Cikin nan ya fara nauyi zama ya ke min wahala. Ina jin su suna waya da Tahir yace shima ya na kan hanya, sai bayan azahar muka isa Zariya tunda su Abba sun tsaya sun yi sallah Sadiq ya siyamin Tsire da Lemu ni ban ma ciba saboda zuciyata naji ta na tashi. A samaru muka Dauki Tahir, na gaishesa ya amsa a dakile sai dai ya gaida Abba cikin Fara'a. Ni na rika numa musu hanyar gidan Baba Tanko har muka iso. Naga motarsa ma a waje yasa nace musu yana gida, sai Abba yace na shiga nace suna jiransa. Ina shiga gidan da sallama da duka matansa naci karo suma sun yi mamakin ganina. Muka gaisa kai tsaye nace"Baba na gida? Sukace min eh yana gida sai nace a waje ana jiransa nazo tare da baki. Amaryar ce ta shiga dakinsa ta gayamasa ina tsaye ko wurin zama ba su bani ba sai dai naga sai kallona suke yi kamar sun ga bakuwar Fuska. Baba Tanko ya fito yana saka Hula Cikin mamakin ganina yace"Hasiya? Ko ba Hasiya bace? Kai Tsaye nace'Ni ce Baba, ina yini? Bai amsa ba illah ce min da ya yi"Lafiya? Wasu baki ne ke nemana? Nima kai Tsayen nace"Mijina ne da mahaifinsa." Ido ya waro kafin yace"Wai daman auran naki bai mutu ba? Sai da kuma ya fad'a yaga cikin jikina sai ya yi gaba yana fad'in"To to bari naje na gani." Na bisa da kallo ina jin wani abu na sukan raina, gajiya na yi da Tsayuwa har sai da na jingina. Ganin haka ne yasa Amaryan baba ta bani kujeren tsugunno na zauna ina jin bayana sun kara kagewa. Achan waje kuwa Baba Tanko na fita wazai gani? Sai yaga Alhaji Sulaiman Shinkafi Surukin Alhaji Jibril. Ya bashi hannu suka ka gaisa lokaci d'aya yana fadin"Ah wa na ke gani kamar Alhaji Sulaiman? Abba ya yi mirmishi kafin yace"Ni ne, kamar yan'uwan Alhaji Jibril na Zariya ko? Baba Tanko jiki na rawa yace"Ba Shakka baka manta ba? Ya fad'a ya na kallon su Sadiq wanda ke sanye da Shadda Deep Blue da Hula Tahir ma manyan kayane ajikinsu nan take ya gane su. Cikin mamaki ya kalli Abba yana fadin"kada dai kace min wannan d'an ka ne? Abba ya kalli Sadiq kafin ya yi mirmishi yace"Eh yaron wajena ne." Baba Tanko sai ya kasa mgana, jiki na rawa ya Bude musu falonsa na waje suka shiga. Bayan sun gaisa sai gashi ya Dawo cikin gida yana rawan baki a kawo Ruwa ya kalleni zaune ya na fadin"Ke ashe mijin naki surukin Baban ki Jibril ne? Gidansa ai Mubarak ya Dauko mata." Ina jinsa bance masa komai ba matansa ne ke ta mamaki, suna ta neman jin mgana a bakina na yi musu gum. Abba ne kadai ya sha ruwa ban da su Sadiq bayan an kara gaisawwa Abba ya kalli Baba Tanko Lokaci daya ya na nuna su Sadiq kafin yace"Ina fatan ka gane su ko? Baba Tanko yace"Tabbas na gane su shekaru uku haka nan suka zo na Daura masa aure da Daya daga cikin ya'yan dan'uwana da ya rasu cikin Shedu masu yawa" Abba ya jinjina kai kafin yace"Daman tabbacin hakane na ke so na samu, Saboda alokacin da ya yi auran bai sanar dani ba sai daga baya." Baba Tanko ya rike baki kafin yace"Kaji ko? Daman sai da na tambayesa, domin nasan da sanin ku dai bazaku bari ya auri bakar tsiya ya kawo muku cikin zuru'a ba" Abba ya yi mirmishi bai yi mgana ba sai kawai Baba Tanko ya gyara zama yana ba ma su Abba labarin irin bakin tsiyar Hasiya da maganar cewa ita ta yi sanadiyar mutuwar dan'uwansu bayan ya rasa komai. Tahir ya kalli Sadiq alamun kadai ji ko?shi kuma sai ya yi kamar bai gani ba. Abba ne ya dakatar da Baba Tanko da cewa za su tafi, 10k ya ijiye masa a gabansa sannan ya mike. Har waje ya rakosu kamar ya yi musu Sujjada, Sadiq ne yace a kira ni mu tafi sai gashi ya shigo zakada zakadan yana fadin na taso suna jirana. Na yi ma matansu sallama na fito sai gashi yau nice Baba tanko ke sakama albarka Harda Allah ya Saukeni lafiya. Daganan har gida suka kaini, Sadiq kunyar tasa bai shiga ba sai da Abba yace ya taikamamin da jakata mana. Sannan ya fito daga Motar Ni kuma sai na Roke Abba ya shigo yaga dakina ko ruwa ya sha. Abba bai yi gaddama ba ya Bude mota ya fito kuma yace Tahir yazo shima ya shiga. Sai ga Abba da Tahir a falona jikina na rawa naje na kawo musu Ruwa, Abba ya sha shi da Sadiq Tahir kuma yace shi baya jin kishi. Abba ya saka albarka ba jimawa yace bari su kama hanya tare da Tahir suka fita Assadiq kuma sai da ya Tsaya ya Rumgumeni ya sumbaceni. Sannan yace na kula da kaina zamu yi waya. Nice har waje na rakasu sai da naga Fitar motarsu layin sannan na dawo cikin gida Maman suhailat nagani Bakina na rawa nace mata Baban Assadiq ne da abokinsa suka kawoni gida. Sai ta faramin fad'a ashe ba na garin ammh shine ban ce zan yi tafiya ba kamar ana zaman gaba. Sai na fahimci laifina na kuma bata Hakuri. Ranar na kwana cikin Farimciki ko bakomai abubuwa suna Faruwa A yadda ban yi Tunani ko tsammani ba. Sai dare muka yi mgana da Assadiq yace sun sauka lafiya shima gobe zai koma Abuja Saboda aiki. Anty Surayya ma ta kirani ta na min bangajiya. Ranar na yi barci harda makara, wayar Safiya ce ta tadani ma, ta na gayamin an kafa mana Time table zamu fara jarabawar Secomd Semister shine ta ke cemin ta Turamin na duba nagani. Tashi na kenan ruwan zafi kawai na Dafa nasha Tea sai ga Ramatu tazo. Naji dadin zuwanta ita ta yi min share share ta dafa mana abincin rana. Sai bayan mun zauna mun natsa ne na bata Labarin duk abunda ya Faru har na zuwana Gusai da dawowar da su Abba suka yi dani jiya. Ramatu ta jinjina kai kafin tace"Ni fa daman na yi ta tunanin Mijin ki yafi karfin inda ya saka kanshi, kuma har Nura ya tabamin maganar jikinsa bai nuna Daga kauye ya ke ba." Cikin gyad'a kai nace"Ni ina na Fahimta na Dauka, duk abunda ya Fadamin gaskiya ne. Sannan bai taba nuna min abunda zan gane wani abu ba" Ramatu tace"Ammh gaskiya na yi mamaki, sai fa kin yi hakuri kin kuma Dage da addu'a domin kinsan in mata suka yi yawa a gida sai a hankali, fatana dai Allah yasa maman nasa ta yarda ta karbeki." Na amsa mata da Ameen ina bata Labarin yadda Assadiq ya tsayamin a gaban yan'uwantsa Ramatu tace"Kaji namijin gaskiya da gaske ya ke yi yana sonki Hasiya." Ta dade sai la'asar ta tafi bayan mun sha Hira ta yi ta bani Shawaran na kwantar da Hankalina kada na saka Damuwa araina. Tazo a jiya washegari yau Adda Fati tazo itama yadda na gayama Ramatun haka na maida mata. Ita kam ta na ta jinjina abun har da zuwan mu gidan Baba Tanko ina fad'amata yadda Baba Tanko ya yi min. Cikin yar dariya tace"Bai taba Tunanin zaki samu miji kamarsa ba ne, lalle wani aikin sai Ubangiji. allah ya huci zuciyar maman tasa ya Daidaita tsakanin ku gabadaya." Itama Addu'an tace na Cigaba da yi, kuma tace na kira Amma na yi mganar da ita. Haka ko akayi a daran na kira Amma na gayamata komai. Mirmishi kawai ta yi kafin tace"Allah ya kauda Fitina Hasiya, ammh in sha Allahu  ina ji ajikina Asssadiq ne mijinki har mutuwarki." Acikin raina sai na samu kaina da amsawa da Ameen Ameen. Itama dai tace min na yi addu'a sannan kada na shiga damuwa Saboda abunda ke tare dani. Haka na cigaba da kula da kaina Gefe daya Assadiq na kula dani Tunda koda yauahe muna tare a waya. Tuni mun fara jarabawa hakanan na dage da karatu ba wasa tunda muna gama Jarabawar Nce3 first Semister zamu tafi Tp ne, ina ta Tunanin yadda zan yi Tunda a lissafina na haihu a lokacin. Anty Surayya ma ta na kira na muna gaisawa, Har Saliha ta kirani mun jima muna mgana da ita, itama ba ta nuna min kyama na ta kuma saka ma lamarin albarka. Ban kuma karajin yadda suka kare ba, ko shi bai yi min mganar ba. Ballatana nasan matsayan Umma da kuma ita kanta Sultana. Shiyasa  nima sai ban yi masa mgana ba abunda ba'a so kaji gwara ka yi shuru da bakin ka kada ka zake kuma da yawa." ******** Baba Tanko da kansa ya kira Alhaji Jibril yana fad'a masa zuwan Alhaji Sulaimam da mganar auren d'ansa da Hasiya. Ya ji mamaki kai Tsaye ya kira Abba yana tambayansa ko gaskiya ne abunda yaji ?shi kuma yace masa hakane. Har Abba ya na masa Tsiyan cewa sun had'a zumunci ta bangare biyu. Alhaji Jibril cikin bakin ciki yace"Alhaji ka kosan labarin yarinyar nan? Ko baka san cewa ta na da bakin jini a tare da ita ba, duk wanda ya aureta ko mutuwa ko rasa lafiya ko Dukiya." Abba ya yi mirmishi kafin yace"Duk na san da wannan." Alhaji jibril yacce cikin mamaki"Kuma ka amince da auran Danka da ita? In wani abu ya same shi fa? Ga shi shi kad'ai gareka namiji." Abba ya kateshi da Fadin"Babu abunda zai Faru face abunda Allah ya Rubuta mana, kada wannan ya Dameka Alhaji." Da haka ya kashe bakinsa har suka gama wayarsu Alhaji Jibril ba shi da wata fara'a a yanayinsa. Har Mubarak sai da ya Turke yana Tambayansa yace shi bai sani ba Salima bata gayamasa ba, yasan dai taje kaduna Saboda ya kara samun Tabbaci yace Mubark yazo da salima gidan. Bayan sun zo ya zaunar da ita yana mata Bin diggi, ita kuma ta fayyace masa duk abunda ya faru, har ta fadin"Babu wanda ya yarda da auran nan Daddy,  Umma ma tace sai ya zaba ko sultana ko ita wannan Asiyar" Alhaji Jibril yace"Uhm Ina tsoron abun da zai Faru da Abubakar ne." Shi har acikin ransa bai yarda da babu Canfi ba Billhaki da gaskiya shi yana Tsoron kada wani abu ya  faru da Abubakar Alhaji yazo sanadin abun ya rusa shi. Shi ai da ya shiga uku domin ya fara hango ma kansa abunda ya Dad'e yana Buri. *Janafty* *TMWB3K09* *TMW is a paid Novel, Pay 500 for regular or VIP N1K, Via 0552179550 Jamila Umar Gt bank, 09069067488* ‎Open this link to join my WhatsApp Group: https://chat.whatsapp.com/IhAz8h8nRy250ZnGGXwM65 Muna cikin jarabawa aka shiga watan azumin Ramadana, ni dai ina ta lallaba Rayuwata tunda yanzu na riga na zama kaya, ina matukar shan wahala na jeka ka dawo saboda makaranta Allah yasa ma ba kullum na ke gwada azumin ba, na fi yi in ina gida shima ba kullum ba, kuma a boye in Assadiq yaji sai ya kama min Fad'an nasan halin da ni ke ciki sai kuma na matsama kaina? Alhalin Addini ya riga ya saukaka mana. Assadiq har cewa ya yi ko na hakura da Jarabawar bayan na haihu jariri ya yi kwari sai na koma daga baya sai na yi Difaring ni kuma naga duk wata Sabuwar Wahalace nace ya barshi zan rika kokartawa. Hakanan na ke zuwa da Katon ciki gaba ina tafiya a tale kamar wata yar kaciya, aikin gidana kam tuni na yaye shi sai in Habiba tazo ne ta kan taimakamin Tunda cikina yana cikin Watannin fitowarsa Duniya ne. Assadiq duk bayan sati biyu ya ke zuwa ya ganni, in kuma yana wajen aiki ko da yaushe muna tare da juna ta waya. Ba abunda zan ce ma Anty Surayya sai Godiya domin ta nuna min dukkan kauna, ita ta yi masa maganar Kudin kayan jariri ya ba kuma bata ta sDiyamin komai har da kayan da zan yi Fitan suna dashi. Kuma sai da ta turomin kayan na zaba duk da kuma nace basai ta yi hakan ba, zata kirani bayan kwana Biyu taji lafiyata ita ta kara karfafan gwiwan ma kada nace zan zauna a gida na cigaba da zuwa makaranta na Saboda hakan zai taimakamin na samu sauki wajen Haihuwa. Amma na lissafe da wattanin Cikina ta kuma bani tabbacin Adda zata zo ta zauna dani, Da ya ke ma Addan na ta fama da Ciwo yanzu Amma ita kuma sai ta yi lafiya. Da watan azumin nan babu abunda Assadiq bai ijemin na kayan abinci ba, sai ma ina kyauta da shi kuma sai da na tambayeshi ya bani izini. Na dibarma Adda Fati kayan abinci har maman suhailat na ba ta, ta na Godiya Ummi dai ban bata ba, tunda Tuni huld'a a tsakanin mu ta jima da yankewa sai dayan matar ne na ba ma wa kawai. Sannan na Diba nace Habiba ta kai samaru dogon gida wajen maman boy, tunda yace a yi sadaka ga mabukata ne. Da ya ke ba su yadani ba Lokaci bayan Lokaci suna kawo min ziyara ne, ni ce ma dai sau daya na taba zuwa anguwan tun bayan aurena da komawar Amma gadan mallam mamman. Bamu muka gama jarabawa ba sai da aka shiga goman karshe na watan azumin Ramadan, Assadiq yazo sau biyu ya dubani ya kuma yi min Weekend, sai dai abun da ke bani mamaki ya rage zuwa Gusai Kamar baya ina tsoron kada ace saboda ni Umma ta raba shi da matarsa. Ina so na tambayesa ammh kuma wata zuciyar na hanani ganin kamar ba Hurumina ba ne, kada kuma yaga na tsallako abunda bai shafeni ba. Hatta kayan Sallar da zan yi fitar Idi da shi yace yana Gusai Big sis duk ta karba kudi ni da Sultana tace zata siyamana. Jin ya ambaci sunan Sultana sai na samu salama araina nace suna tare kenan har yanzu, na manta ko basa tare kanwa take a garesa zai iya yi mata komai da yaya ke yiwa kannensa. Salla saura kwana uku Assadiq ya kirani yace gobe yana tafe na shirya tare zamu wuce gusai chan zamu yi sallah. Duk da har acikin Raina ban so hakan ba , sai dai ban iya ce masa komai ba da yaga na damu sai ya fara lallashina yana nuna min kada na damu yan'uwansa ne ya zama Dole mu'amala ta irin wannan salla ko wata Hidima ta rika had'amu ta hakane har watarana zamu samu Fahimtar juna. Ba ni da yarda zan yi, hakanan na kira su Adda Fati ina gayamusu ita kuma tace miye aciki naje cikin Dangin mijina na yi sallah Tunda haka ya ke so, Adda Rukayya ce da muka yi waya ta rika masifan kada naje a wulakantani fa, tunda ai Adda Fati ta gayamata yadda komai ya Faru. Sai na nuna mata ba wanda zai min wulakanci matukar Assadiq na tare dani, har Amma sai da na kira na gayamata ita dai Fatan alheri kawai ta yi mana. Kafin ya iso duk na had'a abunda zan Bukata da yamma ya iso dakyar na iya Dama masa kuni, shima sai ya tsinke zubarwa na yi Maman Suhaihat ce ta bashi abun bude baki tunda ni azumin da na yi duka duka bai wuce goma ba. Washegari kuma Tun safe muka Dauki Hanya Tunda da Motarsa ya zo,  da na gaji da zama yaga ina ta faman Mutsu mutsu sai muka Tsaya ya Budemin baya na shiga yace na kwanta na Huta shi kuma ya koma gidan Gaba yacigaba da Tukinsa. Da wuri muka isa gusai Shashen Umma muka fara sauka, kuma kamar yadda na Lura kowa yasan da zuwana Tunda shi Assadiq din ya tabbatar musu anan zamu yi sallah. Na dauka zuwa wannan Lokacin Umma ta sauko ashe abun ba haka ba ne, da muka shigo ta na zaune afalonta ita da Sultana suna Sauraran wa'azi a tashar Sunna Tv. Sultana na Sanye da Atamfa Doguwar riga ta na ganinmu mun shigo Umma tace ta tashi ta shiga ciki. Zan durkusa na gaisheta Assadiq yace na zauna saman kujera daman kuma in nace zan duka to aiki ne babba na jama kaina. Dagani har Assadiq Umma bata amsa gaisuwarmu ba. Sai ma wani kallo da ta yi mana ta Dauke kai. Dagani har shi sai muka yi shuru muka kasa mgana , ni kaina a kasa ina ta fama da faduwar gaba. Shi kuma yana Tunanin Fushin Umma zuwa yanzu ya yi yawa gaskiya. Shi a ganinsa tunda ya gane kuskurensa to ta yafe masa kamar yadda Abba ya yi, sannan ta zaunar da shi su yi mgana ta Fahimtar juna. Zuwa lokacin Har chan shinkafi su san da Labarin auransa kuma sun kikkirasa sun yi masa Fatan alheri. Baba Shitu kuma mahaifin Sultana shi da kanshi ya kirasa ya fad'a masa abunda Sadiq bai sani ba ita Sultanan ta kirashi ta na kuka ta na fad'amai wai Sadiq yaci Amanarta sai da ya yi mata Fata fata sannan. Kuma ba wanda yasan Umma ta barota da gidan mijinta ta dawo gabanta da zama ya'yanta na zugata. Abba kuma har alokacin bai ce mata komai ba Sadiq ya kirasa ya na gayamasa Umma bata Daukan wayansa ko zai yi mata mgana? Abba yace ya kara bata Lokaci ta Huce Tukunnah. Kamar daga sama naji Umma tace"Ke bakar Annoba tashi ki fita zan yi mgana da d'ana." Haka ta fad'a kai Tsaye Lokaci d'aya ta na Hararana. Da Sauri na mike har sai da bayana ya amsa, Shima mikewar ya yi Umma ta dakamai Tsawa kafin tace"Koma to ka zauna Bita zai zai." Ba shi da yadda zai yi sai ya koma ya zauna sannan ya kalleni ya na fad'in"Ki shiga bangaren Innani ko bangarem mama" Ban ce komai ba na kama Hanyar Fita shi kuma sai ya daga murya ya na fadin"Kin ji ko? Sai na juyo ina daga masa kai idanuwana fal da kwallah. Na jima a haraban gidan na rasa ina zani sai da na gama kukana na share kwalla sannan na nufi bangaren Mama. Kaamar Daga sama ta ganni farko Siyama ce zaune a falo  ammh yarinyar nan kallo wulakanci ta yi min sai ni ce na gaisheta sannan nace mata wajen Mama nazo, shima sai da taga dama sannan ta tashi ta shiga ciki ta yi ma Maman mgana sai ga su sun fito tare. Ita da Fara'a muka gaisa fad'i ta ke yi" yanzu kuka iso kenan? Ina shi magajin gidan? Kaina na kasa nace"Ya na wajen Umma, shi yace na zo nan na zauna." Mama ta jinjina kai kafin tace"Allah sarki sannun ku da zuwa ya nauyin jiki? Kai wannan cikin naki akwai girma wa ya ga Runduna." Kaina na kasa ban yi mgana ba, sai faman hira take min ta min Tambayoyi ni kuma bani da sakewa yasa na ke amsata daya daya. Ni ce naga ko ruwa ba ta bani ba sai nace mata zan sha ruwa. Cikin yake tace"Af nafa manta ku bakwa azumi,  Siyama" Sai ta fara kwalama Siyama kira sai gashi ta fito ta na wani Tura baki Mama tace ta kawomin Ruwa. A wulakance ta kawomin Ruwan gora kuma don mugunta mai sanyi, ba ta ko Duba Halin da ni ke ciki ba. Kuma babu ko karamin kofin da zan sha, Kuma gashi ina jin kishi hakanan na sha kad'an na ijiye. Daga karshe da Mama taga na kasa sakin baki na bata labari sai ta shige ciki su ka barni anan kamar wata almajira. Gashi Fitsari ya matseni na rasa yadda zan yi, ina zaune kawai ina ta sharan kwallah na tausayin kaina a baya ina Murnan na fita daga cikin Tsaka mai wuya ashe tsuguuno bata karemin ba. ****** A falon Umma kuwa bayan Fitata sai da Umma ta gama shanya Sadiq zaune a gabanta sannan ta gyara zama ta kalleshi Lokaci d'aya ta na fadin"Abubakar dago nan ka kalleni." Ba musu ya dago yana kallonta Fuskarta ba Fara'a tace"Wacece ni hala a wajen ka? Cikin mamakin Tambayarta yace"Ke din mahaifiyata ce." Wani mirmishi Umma ta yi kafin ta daga baki ta kira sunan Sultana ta amsa sai gashi ta fito. Gaban Umma ta durkusa ta na cewa gata, Umma ta kalleta yadda duk ta rame a tsaye, suma cikin satin da ya fita suka gama WEac Sai neco. Duk ta rame ta Lalace sannan ba ta da wani Walwala bata da aiki sai kuka. Itace ya kamata ta share mata hawaye Tunda dai ba ta da wata Uwar da ta wuceta. Nuna masa ita ta yi kafin tace"Ita kuma miye nata matsayin a wajen ka? Sai da ya dago ya na kallon sultana wacce ta kauda kai gefe kamar bata son kallonsa. Cikin sanyin murya yace"Ita d'in kanwata ce sannan kuma matata." Umma ta jinjina kai kafin tace"Shine ka maida maganata banzaa ko Sadiq? Ba na gayamaka ka zaba ko sultana ko wanchar bakar Annobar ba? Ammh Saboda Alhaji ya baka Dama sai ka saka kafa ka shure mganata ka yi tafiyarka tare da matarka kana so ka nuna min abunda ka ke nufi ko? Zai yi mgana ta daga masa hannu a Fusace ta na cigaba fad'in"Bana son jin komai daga bakin ka, yanzu zaka gayamin meneme manufarka? Tunda ka tafi ka barni da yarinya kuma baka min wata mgana ba, in ka zab'i wancan ne sai ka sakarmin yarinya domin tasan ta fara Iddarta." Baki ya saki kafin yace"Me ya kawo kuma mganar Saki anan wajen kuma Umma? Umma ta balla masa Harara kafin tace"Bansani ba, sallamamme mara Tunani ai na riga na fada maka baka isa ba. Indai ka zabi zama da wannan Annobar to sai ka sakarmin y'a kaji ma na gayamaka." Shuru ya yi kansa na kasa kafin yace"Umma ba maganar saki Tsakanina da Sultana ballatana Siya, dukkansu ban aure su domin na sake su ba." Umma ta harzuko kamar zata dakesa ta na fadin"To wlh ahir dinka, kai da dauko bala'in sai dai ya kare maka ammh bazan bari diyata ta zauna da kai ba, tunda ka zabi Ita Bakar Annoba to ka shirya sakar min yarinya kaji ma na rantse." Cikin mamaki yace"Umma kada ki yi saurin Rantsuwa fa? Umma tace"Nace wlh tallahi Rantsuwan d'an musulmi in baka saki wannan annobar matar da ka jajibo ba, to auren ka da Sultana na Haramtashi." Baki sake yace"Umma kada ki zo ki yi kafarra gwara ki janye rantsuwan ki domin na baki tabbacin dukkansu ina son su ba kuma zan iya Rabuwa da d'aya saboda d'aya ba." Mamakinsa ya kama Umma daman ai tasan halinsa ba'a kadashi a mgana. A fusace tace"Sai kuma ka yi, tashi ka bani waje ni na riga na gama mgana." Kin tashi ya yi sai ma ya gyara zama yana fadin"Umma ki yi hakuri don Allah, nasan na yi ba daidai ba ammh tunda nagane kuskurena sai ki yi min afuwa don Allah." Umma saboda ma tagaji da jin mganarsa sai kawai ta kallo sultana ta na fadin"Ke tashi ki karamin karan Tibin nan ki shiga ciki." Ba musu Sultana ta mike Idanuwanta har sun tasa saboda kuka ta kara karan talabijin din ta wuce salau salau ta koma cikin daki Sadiq ya bita da kallo. Kafin ya girgiza kai kawai, bai tab'a Tunanin haka yarinyar ta yi nisa ba sai yanzu, tun bayan Faruwar abun bata bari sun yi mgana ba ya yi ta kiranta bata dauka ba, har Texts ya tura mata na ban hakuri duk da shi a ganinsa bai yi mata wani laifi ba ammh yarinyar nan ta yi masa banza. Sai cikin satin nan yaga ta turo masa sakon wai ta jisa shuru ta na jiransa. To alokacin ya dauka ta sauko ne za su yi magana sai ya kirata kawai sai ta rika latsa masa Busy. Shi kuma da ya Fahimci ba ta da kunya sai ya kyaleta shekaranjiya kuma sai gashi ta kara Turo masa wai tana so tasan matsayinta. Bai yi mamaki ba daman Big sis tace su Sadiya ke kara zugata ita da Umma. Kuma daman yasan kowa acikin su musamman Sajida da saboda munafunci bakinta ya yi tsini uwar gulma. In ta zauna ta na Biye musu ita ta sani shi dai Allah na gani akan abunda ya aikata na raya sunna ma'aiki, kuma yace yasan bai kyauta ba kuma ya ba da Hakuri ammh yarinyar nan na neman kuresa. Kawai sai ya tura mata da sakon cewa amsar matsayinta na wajenta, duk matsayin da ta yi ma kanta shi a wajensa daidai ne, kuma ya na da tabbacin su suka zugata ta Rubuta masa haka. Bai hakura ba, ballatana ya Saduda haka ya zauna ya na ta ba ma Umma Hakuri ita ko ta na zaune ta na masa wani kallo. Sai da taji yace"Umma yanzu in kika ce sai na saki Siya  ina kike so taje da wannan Tsohon cikin? Kuma fa bai hallasta saki da ciki a irin wannan Lokacin ba." Umma ta daga masa hannu a Fusace kafin ta mike taje ta kashe talabijin da kanta sannan ta Dawo ta zauna ta na fadin"Maimata abunda ka ce yanzu." Kansa na kasa ya maimaita Umma ta fara fad'a ta na fadin"Ah ba Siya ba Siyoyo kaji min mara kunya, ina ruwana da cikin jikinta kai ke da matsala dashi, abun takaici ma mallam wai ka rasa waxaka aura sai bazawara wacce ta gama yawon dakuna? Kuma nasan kasan  bakar Annoba ce, kowa na gudunta ammh da ya ke kai shashasha ne sakarai sai ka kwasa ka kawo mana cikin zuru'ar mu ko? Ta fad'a ta na kallonsa cikin Takaicinsa. Sadiq daman yasan haka zata Faru sai ya yi shuru ya na jin Umma ta na ta zagin Hasiya ta na aibata ta. Ita kam ai sha kumdum ne bazai iya kare Siya a gabanta ba. Ammh dai bazai ki gayamata abunda Allah yace ba. Cikin sanyin murya yace"Umma miye Laifin zawarawa ? Su ba Mutane ba ne? Sannan me yasa a ke son ware su daga cikin mata? Ai suma Mutane ne kuma ba su suka kaddaro ma kansu mutuwar aure ba kaddaran Allah ne, Umma ko acikin ya'yan ki suma Allah zai iya jarbtan daya daga cikin su da Mutuwar aure in wannan ya faru sai ki ce mene? Umma ta yi hangam da baki ta na kallon Sadiq ya na cigaba da fadin"Kuma Umma sunan nan da kike kiran siya da shi bai kamata ba, ba kyau musulmi ya rika aibata musulmi  dan'uwansa balle kuma ya yi masa Dariyan kaddaransa  dalili shine shima bai wuce kaddaran haka ta fada masa ba, kuma Umma duk fa karya ce ba wani Canfi a addinin mu, bamu san shi ba, Qur'ani ya koya mana sanin Tauhidi da iklasi kuma ni a iya ilimin da na ke da shi nasan cewa Wani abu bai isa ya samu wani bawa ba face abunda Ubangiji ya Shirya masa." Umma sai kallonsa ta ke yi kamar ta kai masa duka, Sai da taga ya kara wani gyara zama zai kara shiryamata magana Fusace ta dakar dashi da cewa"Kai dalla gafarachan, ni zaka zo ka zauna da d'an iliminka na cikin cokali kana gayamin nima za'a iya sakar min ya'ya su zama zawarawa ? Cikin mamaki yace"Ni fa ba." "Ka rufemin baki nace ko? Karya na yi maka ba haka ka zauna anan wajen kana fad'amin ba, tashi ka fita ni bazan gani ba Tunda mace ta saka ka fara musu da uwarka da yan'uwanka daman Tuni ka nuna musu iyakarsu ai sai kaje ita ta zame maka uwa da yan'uwa" Zai kara magana Umma ta mike ta na fadin"Kada ka fita di'n , ni bari na bar maka falon." Jiki a sabule ya fita daga bangaren Umma Abba baya nan ammh sun yi waya yana nan dawowa. Ya dauka ina bangaren Innani sai da yaje yaga ba na nan daga ita sai Farida. Daman sanda aka yi wannan Cases din bata nan taje ganin gida chan Shinkafi. Innani ta rika ina ta saka dashi shi kuma yana mata cin magani. Kula da hakan da ta yi ne yasa tace"Nifa tuni na Saduda na bi Allah Tunda Sulaimanu ya yi min nasiha ina ni ina ja da Abunda Allah yace ayi, Uhm ni wai ita sulsanan Salamatu ta rike ta ta ce bazata koma gidan ka ba ne magajin gida? Kai Tsaye yace"Haka tace" Innani ta yi shuru kafin tace"Ba abun na yi mgana ba yanzu sai ace na so bare naki d'an gida." Kai Tsaye Assadiq yace"To gwara ki yi shurun zai fi miki alheri." Daga haka suka cigaba da Hirarsu tace ina Matar tasa yace yana ga tana bangaren Mama. Innani ta tabe fuska kafin tace"Da ba nan ka kawomin ita ba, wai ni yaushe ne zata haihu har yanzu shuru ban ji an ce ta sauka ba? Sadiq yace"Ki tayata da addu'a Innani ta na watan haihuwanta ne" Innani ta fara jero addu'o'in Ga Hasiya Sadiq na amsa mata da Ameen Da yaji dadi kai Tsaye yace"Ke zaki zo mata ma zaman arba'in na Jego." Innani ta washe baki ta na fadin"Allahu akbar Allah ya nuna min ranar da wannan albarka zata sauka a gidan Magajin gida. Ya jima a bangarenta sai da Abba ya kirasa yace ya dawo sannan ya yi mata sallama ta na ce masa ya kawo mata Hasiya bangarenta ta zauna har ta na rage murya ta na fad'in Tunda salamatu dai ta cire Allah a ranta ba mutumtata Baiwar Allah zata yi ba. shi dai bai ce komai ba sai Dariya kawai da ya yi. Bai nemeni ba, sai da yaje shashen Abba suka gaisa ya kuma zauna ya karanta masa komai da Umma ta tareshi da shi. Abba ya yi mirmishi kafin yace"Rabu da ita, ina mai tabbatar maka itace zata yi kaffara ammh kamar yadda na fad'amaka ba wacce zaka saka saboda wata." Sadiq yace"To Abba ya zan yi? Umma taki fahimtata." Abba yace"To ka nemi matarka ka lallasheta mana." Da sauri yace"Duk su Sajida sun gama zugata bata ko daukan wayata, Allah Abba ka hana su zuwa gidan nan basa yad'a komai sai sharri akaina da Matata." Abba na dariya yace"Ka kyalesu duk su yi su gama, ai ba su isa su ja da ikon Allah ba." Jin abunda Abba yace ne yasa sai ya bar mganar. An riga an yi sallar azahar Abba kuma ya tsaya a chan ya yi tashi, shi kuma sai ya yi nashi a bangaren Abba. Sai da ya idar da sallah ya Kira Big sis yace sun iso shi da Hasiya Tun dazu. Surayya tace shine bai kawo ta gidan ta ba? Shi kuma yace ya na Tsoron ya kara yin laifi. Dagachan Bangaren Surayya tace"Ba wani laifi, bazata sake acan ba ne, zan zo anjuma sai mu taho tare wajena daganan ma sai taga kayan da na siya mata ko? Kai tsaye yace"Shikenan sai ki zo kawai ki Daukemu tunda nima Umma ta daina ya yina." Surayya tace"A'a chan kai da Mamanka ni kanwata kawai zan dauka kaji ma na gayamaka." Daga haka ta katse wayarta yana mata Dariya. Sai da ya koma Bangarensa sannan ya kirani a waya yana jin kunya shiga Dakin Mama. Ni ko sai da na yi mgana aka bani daki na shiga na kama ruwa na yi sallah ina zauna na yi tagumi kiran Assadiq ya shigo wayata. Shi ya debemin kewa da Hiransa yana bani Labarin yadda suka yi da Tahir ya kirasa yana tambayansa wai daman ciki ya yi min? Sadiq yace"Eh mana na yi kankanta da yin cikin ne? Tahir ya yi tsaki kafin yace"Dan iska, kawai." Na yi ta dariya ina fadin bai kyauta ba, shi kuma yana cemin Tahir ne yaja domin ya yi masa tambayan Renin wayau. Sai da muka fi awa muna waya sannan yace naci abinci sai na yi masa karyan naci, jin haka yasa yace na kwanta na huta. Daganan muka yi sallama kamar kuma yadda yace sai na kwanta sai barci Saboda gajiyan mota. sai bayan la'asar na tashi Lokacin ne naji ana ta Hidima na gobe sallah. Ina bangaren Mama har bayan shan Ruwa sai lokacin Siyama ta kawomin abinci ta na min wani kallo. Tuwon shinkafa miyar egusi, sai kuma Ferfesun kayan ciki da lemun kankana. Naci kad'an saboda bana jin yunwa sai na sha lemun, bayan na idar da sallah na kira Assadiq na yi masa barka da shan Ruwa sai yace na fito zamu gaisa da Abba. Da Tulin Cikina gaba na sanyo Hijabi na samu Mama da Siyama afalo nace mata Assadiq na kirana zan je na gaida Abba ta bi ni toh shikenan. Ina fita haraban gidan na Hangosa shi yazo ya rikeni har bangaren Abba. Muka had'e da Umma achan ta na had'a ma Abba kayan Bude baki.. Zan duka yace na zauna a saman kujera na zauna muka gaisa cikin Sakewa yana tambayana ya karatu nace masa mun gama jarabawa. Kai Tsaye yace"Ki saki jikin ki fa, nan ma duk gida ce kuma zaki ki ji dadin salla tare damu." Mirmishi na yi kafin nayi masa godiya umma kuma tana gama abunda zatayi ta fice ko amsa min barka da shan ruwan da na ke yi mata bata yi ba ta Fice. Abba da Assadiq tare suka yi Bud'e baki, ni kuma sai nace bari na taka zuwa bangaren Innani. Na gane gidan yanzu kuma na kai kaina bangaren Innani ina shiga sultana na fitowa ta dawo kai Innani Ruwan zafi. Muka kusa cin karo sai muka tsaya muna ma juna kallon kallo Ni ce ma na kauda shurun ina Mirmishi nace"Sultana." Duk da ina jin wani abu a raina ammh sai na Danne. Ita ko wani irin banzan kallo ta yi min kafin kawai ta bangajeni ta wuce a bakinta naji tace"Banza mai kwacen miji kawai." Ni ba wannan na damu ba sai bangazar da ta yi min kamar bata ga bani kad'ai bace. Bango na Dafe yasa ban fadi ba, na bita da kallo ina jinjina kai. Da sallama na shiga Falon innani suna zaune da Farida. Da farko bata ganeni ba sai da na yi mata bayani tunda itama Faridan bata sanni ba. Aiko sai ta washe baki ta na ta min Dariya ta fara min fira labarai harda na Umma da ta hana sultana komawa gidanta. Tace min"To ni in na saka baki sai ayi cewa na zabe ki naki jikata, kinsan mutane ba'a iya musu. Kuma ni na saduda ne na bi Allah Tunda sulaimanu da magajin gida suka min nasiha na yi shuru da bakina kada na Tofa ace na yi munafurci." Ni dai sai dariya na ke yi mata, Innani akwai dadin zama. Dan zaman da na yi a bangarenta na sha Labarai kala kala harda na chan mutanen shinkafi. Sai zuwan Surayya ne ya tada Hirarmu tace daga wajen Su Abba take Sadiq yace ina sashen Innani. Ta zauna itama ammh bata dade ba, tace na taso mu tafi na yi ma Innani sallama sai da muka fito ne muka had'u da Sadiq. Sai da na shiga mota sannan suka koma gefe suna mgana da Anty Surayya na wani Lokaci sannan suka yi sallama ya lekoni yana fadin"Siya Good Night" Sannan ya sumbaci goshina Surayya na fadin"Sadiq ba kunya a gabana." Ya matsa baya yana dariya. Tun a mota muka fara hira da Anty Surayya da muka je gidanta ma na jima afalo muna Hira har da mijinta sai da na fara jin barci ta kaini inda na ke sauka tace na yi wanka na Huta. Ta kuma kawomin man zafi na shafa aiko ina yin haka sai barci. Da safiyar idi kuma an tashi da hidima duk yadda naso na taimakamata hanani ta yi, tace na shirya in zan iya mu tafi masallacin Idi nace mata zan iya. Ta bani kayan da Assadiq ya yi min kala uku leshi daya Atamfa biyu. Atamfar na saka an dinkamin Buba kamar an aunani Cif dani. Sai bakin Hijabi sabo saboda Fatata sai ya yi min bakyau kamar wata baturiya. itama ita da mijinta da ya'yanta sun yi kyau sosai shi ya tukamu zuwa masallacin idi. Chan muka had'u da Assadiq da Abba bayan an sauko masallaci sun sha Fararan kaya har da manyan Riguna. Sama sama muka gaisa yace sai ya zo gidan. Da muka koma gida abinci muka ci Sinasir Anty Surayya ta bada aka yi mata, ni kuma bayan na ci na koshi na koma daki na kira yan'uwana da abokan arziki na yi musu barka da Sallah da Ramatu ne muka jima muna waya. Bayan mun gama na ijiye wayar na kwanta sai bayan azahar na tashi Anty Surayya tace na sha barci har Sadiq yazo ya tafi. Sai da na yi salla ta kwasomin kayan da ta siya na jarirai shago guda ina ta kallo ina saka albarka Mun dade muna Hira da ita ta na kara bani baki akan Umma ta na tabbatar da zata sauko watarana. Sai Dare Assadiq ya dawo bamu wani jima muna Hira ba ya tafi saboda na fara jin barci washegari ma Dangin mijin Anty Surayya ne suka zo. Shiyasa bamu je gidan su Assadiq ba sai Washegarin sallah da kwana Biyu. Na sanya leshin nan Shima dinkin Buba ne, ya zauna a jikina sai na sanya Hijabi kalan adon leshin. Muna mota Anty Surayya ke fadamin Saboda ni yam'uwanta wannan sallar ba wanda yazo gidanta. Kuma sun saba a jiya kannen nata suna zuwa wajenta su yini. Muna zuwa gidan ko suna nan a shashen Umma, Sadiya da Sajida sai Sa'adatu Saddiqa kuma Tunda ta koma bata zo ba, ya yi kusa da yawa. Shashen Mama duk ya'yanta ne su Sa'ima da su Shahida har Salima ma tazo sallah. Dukkansu kuma a shashen Innani muka gansu dukkansu kuma na bi su na gaishesu suka amsa min a wulakance, wasu ma ba su amsani ba. Innani kuma ta karbeni cikin Fara'a kamar yadda ta saba min na riko mata Turare daman tundaga Zariya na bata ta karba ta na ta saka albarka su Sajida nata tabe baki. Umma kuma har bangarenta mukaje na gaisheta sai a ranar ta amsamin da lafiya. Daman kuma bangaren Mama muka fara zuwa muka gaisa, Abba kuma baya nan sun fita da Assadiq. Anty Surraya tace mu zauna a bangaren Umma, ita kuma ta bi Umma ciki ban san me suke Tattaunawa ba. Na jima zaune ni kadai sai ga Sultana ta shigo da irin less din dake jikina. Kallon kallon muka yi ma juna ina shirin na gaisheta naga ta yi tsaki ta wuce kawai. Kiran sallar mangariba yasa su Sajida suka baro bangaren Innani zuwa Falon Umma. A d'ayan bedroom din Anty Surayya ta kaini na yi alwala na yi sallah.bina zaune ina addu'a Sultana ta shigo ta yi kuma mamakin ganina sai da ta Tsaya shuru sannan kuma ta koma da baya. Sai da na natsa sannan na fito falon Anty Surayya bata falon ashe waya aka kirata sai ta fita. Ina shigowa falon sai na tafi kujeran chan nesa da su zan zauna har ga Allah ban ga Tahowar Sultana ba. Sai da naji ta min wani bangaza kamar na ranar. Na kusa faduwa da yasa hankalina ya tashi sai da na Dafa kujera. Cikin sauri nace"Sultana kamar baki ganina? Sai gabadaya Hankalin su Sajida ya koma kaina. Kallon cikin ido ta yi min kafin tace"Au Allah? To ban gan ki ba." Sai alokacin na Lura ta sauya kayan jikinta. Batare da na kara mgana ba na gyad'a kaina na koma na zauna ina daidaita yanayina. Sajida ta yi tsaki kafin ta kalleni ta na fadin"Ko da ta ganki ke ya kamata da kika ganta bayan kin kauce mata sannan ki ramkwafa ki gaisheta da ladabi." Sadiya tace"Tabbas tunda ita kika yi ma kwacen miji." Na yi shuru ban yi mgana ba Sadiya ta dakamin tsawa ta na fadin"Bazaki duka ki gaisheta ba? Sai kawai na sauko daga kan kujera na Duka kan kafafuwana ina cije baki na kalli Sultana dake tsaye nace"Ina yini sultana? Idanuwana sun ciko da kwallah.. shewa suka saka gabadayanau suna min dariya. Sajida tace"Kowa ya tuba  don wuya.". Sadiya ta karishe da fadin"Ba lada." Ba su sam shigowarsa ba  ni kaina kamshin Turarensa naji da kuma dagoni da ya yi daga durkushen da nayi. Sai jin muryansa suka yi ya na fadin"Are u ok? Sai na gyad'a masa kai. Shuru suka yi sun sha jinin jikinsu, kallonsu ya yi a fusace kafin ya Tsaida kallonsa kan Sultana da wani hade rai tana marmari da ido. Har gabanta ya taka bayan ya sake ni, ya tsaya kam sannan ya daga hannu ya nunani kafin yace"Kinga wannan? To itace matar da na fara aura kafin ke, saboda haka daga yau ya kamata ki sani tana gaba da ke, ke zaki fara girmamata kafin ita ta girmamaki." Sultana ta kallesa kafin tace"Tab." Ta fad'a ta na Tura baki. Sadiq ya jinjina kai kafin yace"Eh haka nace saboda haka daga yau in kika ganta ke zaki gaisheta ki, ya kamata ki haddace cewa ita na fara aure kafin ke, ni kuma ba sakaran namiji ba ne da zan zauna kina wulakantamin mata ba, Sonta na ke yi shiyasa na aureta kamar yadda kema ina sonki ne yasa na aureki." Sultana sai hawaye ta na so ta saka kuka. Sajida ta gaji da shuru tace"Ammh Sadiq baka da kunya wlh." A fusace ya daga mata Hannu kafin yace"Ban saka da ke ba mallama ki Rufemin baki, ko ina ruwan ki da shiga Hurimin iyalaina.? Ya karishe fad'a yana nuna ta da yatsarsa. Ai sai ta kasa mgana ganin ya harzuka Sadiya ma na shirin magana a harzuke yace"Kada wace ta kara sakamin baki acikin magana ta da iyalaina. In ba haka ba  ran mata zai baci na rantse da Allah." Surayya ta shigo tana gefe ta na mirmishi. Kan Sultana ya koma yana fadin"Sabosa haka ki shiga taitayinki, in kikace zaki yi ma matata fitsara maganinki zan yi bana son reni kin sani." Sultana ta mike ta saka kuka ta na Fadin"Ai ba sai ka nun ma duniya baka sona ba, auren hadi aka yi mana shiyasa ka ke kare ma wannan banzar matar taka mai kwacen miji kawai" Taso mata ya yi kamar zai Daketa ta yi baya sai kawai ga Umma Tsulum a falon. Shi ya hanasa kara wani motsi ni kaina gabana sai fad'uwa ya ke yi Sajida na ganin Umma ta Nufeta ta na karanta mata Assadiq ya zagesu saboda ni. Har yana nufar Sultana zai daketa. Umma bata wani tsaya Bincike ba ta nuna ma Sadiq kofa tace ya fita ya bata wuri yana Hucin ta hanashi mgana ya fita. Ni kuma ina Tsaye kafafuna na rawa Surayya ta taso ta wankeni Umma ta d'aga hannu ta na karisowa cikin Falon lokaci daya ta na kallona kafin ta juya ta kalli Sultana tana fadin"Share hawayen ki, matukar ina raye ba wanda ya isa ya Tozarki." Sultana ko kuka take yi sosai daman ganin kayan mu iri daya yasa su Sajida suka kara Zugata da cewa ita bai Dauketa da Muhimmanci ba muraranta ya ke nuna yafi kaunata sma da ita, ita kuma bakin kishi ke dawainiya da ita. Umma ni ta kalla a fusace kafin tace"Ai in baki had'a fada tsakanin yan'uwana juna ba baki ci sunan ki  bakar Annoba ba, kin ji kunya kuma kin yi asara ke yanzu a dad'in ki ne ki zo ki raba kan zuru'a? Ki saka d'ana ya na jayayya dani sannan ki sakashi yana Sa'insa da yayyensa to ki saurareni dakyau har Abada bazan taba karbanki a matsayin matar Abubakar ba, Sultana na sani kuma in dai ke ya zaba wlh sai dai na sallama miki shi, shi kadai Annobarki ta kona sa, Fita ki barmin falo kafin raina ya baci na saka ayi miki koran kare." Daman tun da ta fara mgana na fara kuka ina jin tace na fita na juya ina jin cikina na Juyawa na fita ina kuka. Surayya ta kalli Umma ba dad'i kafin tace"Umma m." "Ke ma bita ki fitar min daga falo." Surayya ta kalli Umma kafin ta kad'a kai kawai ta juya ta bi bayana su Sajida suka rakata da wani kallo aransu suna tunanin Big sis bata kishin Umma. Ta na fitowa ta ganni ina kuka, sai ta rikeni zuwa mota itama ranta a bace yake Sadiq ta kira tace yazo ya Tukamu zuwa gida. Ya shiga damuwa ganin yadda nake kuka sai ya fara cewa ita ta lallasheni. Da damuwa a saman fuskarta tace"Lamarin Umma ya fara nisa, Su Sadiya suna kara zugata ni yanzu kwata kwata ta daina bani fuska." Sadiq yace"Nima wlh abun duk ya Dameni." Surayya ta sauke Numfaashi kafin tace"Mallam na gummi zaka je ka sanar ma abunda ke faruwa na tabbata in ya yi mata magana zata ji." Sadiq yace"Na yi tunanin haka, ammh cewar Abba ne na bata Lokaci Shiyasa ban je na samesa ba" Surayya tace"Ai kada ka jira, ammh kafin nan gobe ka maida Hasiya gida, zamanta a wajena ni kaina Umma ta fara fushi dani kuma bata da sakewa kwata kwata anan." Ya aminta da shawaranta yace haka za'ayi in zai kaini Zariya zamu Tsaya anan Gummi din. Haka ko akayi, tun safe muka tafi Abba kawai da Innani ma yi ma sallama da kanshi ya hanani Shiga wajen Umma, fuskata har ta Kumbura saboda kuka da kuma duka siyayyan da Anty Surayya ta yi min muka taho da su. Sai da muka fara biyawa Gummi Gidan su Umma kamar yadda yace min suka gana da mallam zakari na wajem awa d'aya. Da kanshi ya yi mishi bayanin komai, mallam zakariya na ta fad a yace kuma sai ya saba Umma har Abban ma da ya Biye mata. Sam a gidan ba'a nuna min wani kyama ba nan muka yi azahar muka ci abinci sannan muka dauki hanya. Sai bayan la'asar muka shigo Zariya ganin yamma tayi yace sai da safe zai wuce Abuja. A daran ina jinsa ya Kira mahaifin Sultana shima ya karanta masa abunda ke faruwa. Ran mallan Shitu ya baci yace gobe goben nan zai je ya samu sultana sai ya sab'a mata itama. Sadiq daman so ya ke daga Umma har Sultanan a yi musu fad'a alokaci daya. Kwana ya yi yana lallaahina tare da alkwarin  bazai taba barina ba. Ni na ma b'ata masa Lokaci sai wajen goma ya bar gidan ya kama hanyar Abuja. Sadiq ya fita cikin Damuwa ga koken koken da na kwana yi. Ga kuma matsalan su Umma da Sultana gabadaya sun chazamasa kai. Ya bar kaduna kenan da kad'an baisan yadda aka yi ba motar sa ta kwace masa ba, shi dai yaji mota na Tamaula dashi akan Titi daganan Hankalinsa ya gushe. Yaji sanda motar ta Tsaya ya kuma san ya jisa zaune a inda ya ke jini na bin fuskarsa tunda ya saka Seat belt. Daga nesa nesa yaji ana salati da sallallami tare da mganganun mutane daganan yaji Duniyar ta tsaya masa cak. *Janafty* *TMWBK3010* P *TMW is a paid Novel, Pay 500 for regular or VIP N1K, Via 0552179550 Jamila Umar Gt bank, 09069067488* Duk sammakon da Mallam Zakari ya buga daga Gummi zuwa Gusau sai da ya zo ya iske Mallam shitu ya rigasa zuwa daga Shinkafi domin ana idar da sallar asuba ya kamo hanya so ya ke ya yi abunda zai yi. In ya gama ya kama hanya koma can har kuma yaje ya yi yan Harkokinsa. Sultana sai da ta raina kanta, ta sha Fad'a kamar me, dukanta ne kad'ai Mallam Shitu bai yi ba, bata tab'a sanin cewa ya iya fad'a haka ba Tunda wani abu bai taba had'a su ba, sannan kuma ba ta girma a gabansa ba sai dai zuwa ta na dawowa. Umma kuma sai ta so ta kareta ita ma Mallam Shitu ya kalleta yana fadin"Maganar gaskiya Hajiya ki daina mara ta baya, da ke har ita baku taki gaskiya ba abunda ku ke son ku aikata ba gaskiya ba ne kuma ba Shari'a bace." Sannan ya kara kallon Sultana da ke gefen Umma ta na ta faman kuka, har Abba na wajen shi da Innani tunda a shashen innanin ne ake zaman. Cikin daga murya yace"Ke kuma ki sani in dai kika Boyema zuciya kika ce zaki wulakanta mijin ki, ke ce a kasa matukar kika rasa miji kamar Abubakar ba baki na yi miki ba ammh Wlh tallahi bazaki taba samun kamarsa ba, kuma ina so ki sani bai kamata ki zama Butulu ba, in mahaifiyarsa ta nuna fushi a kansa ta na da gaskiya itace uwa a garesa ammh ke baki da wannan Hurumin tunda kina karkarshinsa ne daidai da rana d'aya in kika sab'a masa sai Allah ya Hukuntaki akan laifin da kika aikata." Sultana na kuka Fuskata duk hawaye ta dago ta na fad'in"Baba aure fa ya yi bansani ba." Dakuwa ya yi mata kafin yace"Kin ga naki, ana rabaki da kiwon awaki kina kokarin gayamin kyalla ta Haihu? Ya yi auren sai me? Ke ki kiyayi kanki ai ita ya fara aura in yaso sai yace ya fasa auranki kuma ba mai yi masa Dole, ammh bai yi haka ba sai ke ce don rashin Mutumcin ki ke har kara fad'in aure ya yi, to ya yi auren sai ki hanasa abunda Allah yace ya yi, ni ai da ya Burgeni ma da uku ya aura sai ku zama ku hu'du naga yadda zaki yi, banda shashanci ko ni Ubanki bayan mahaifiyarki matana Biyu saboda Rashin adalci irin naki don mijinki ya yi aure sai kice zaki fara yi masa rashin d'a." Daga Umma har Sultana suka yi shuru, Umma ranta ya gama baci saboda ta da na tabbacin Sadiq ne ya Kirasa ya fad'amasa kuma taci alwashin zai zo ya sameta sai ya raina kansa. Ita kuma Sultana kukan yadda Babanta ya kasa Fahimtar irin cin Amanar da Yaya Sadiq ya yi mata ne, ammh kuma sai ya zo ya Bige da yi mata fad'a. Fata fata ya yi ma sultana itama Umma ya yi mata nasiha yajawo Hankalinta, ammh duk bata ji ba ta dai nuna kamar ta fahimce shi kuma zata gyara ne. Kafin tafiyarsa sai da ya jaddadama Sultana ta koma dakinta mijinta yau ba sai gobw ba, kuma sannan ta girmama ra'ayin mijinta. in kuma yaji Sabanin haka zai kara dawowa ammh ta sani dawowar bazata yi mata kyau ba. Ko karyawa bai tsaya ya yi ba wajen Goma na safe ya Juya ransa bace shi kam Abba lamarin ya yi masa daidai. Innani kuwa kamar an tsaface bakinta bata yi mgana ba sai dai Mallam Shitu ya sha tabe baki da Harara ta zata zai sako sunanta ne ta yi masa wankan Tsarki duk dai tace ta yafe ammh dai duk da haka dai, sai kuma aka yi sa'a bai sako sunanta ba to ina zai sakota Tunda yasan Halinta. Sultana kuwa bayan tafiyar mahaifinta ta kalli Umma lokaci d'aya ta na fadin cikin kuka"Umma yanzu sai na koma? Umma ta kalleta ita tsabar takaicin da ta ke ciki ya hanata mgana, ta na ganin Sultana na gunjin kuka ammh ta kasa ce mata ci kanki ballatana ta iya lallashinta Tafiyarsa ko awa daya ba'a yi ba sai ga Maallam zakari d'aya daga cikin jikokinsa ya rakosa. Tunda Abba ya kira Umma a waya ya gayamata zuwan mahaifinta nata gabanta ya fad'i saboda tasan halin Mahaifin na su yana da zafi, shifa ba ruwansa komai girman ki kika aikata ba daidai ba gaban ya'yanki zai yi miki Kaca kaca bai damu ba. Shiyasa tunda Umma taji Labarin zuwansa jikinta ya yi sanyi sannan a gefe daya kuma na zuciyarta ta kara Kullatan Sadiq wato itama bai barta haka ba sai da ya had'ota da mahaifinta lalle zai gane ba shi da wayau in suka had'u. Shima a bangaren Innani ya sauka daman ta so tazo d'aya da Innani, itama sosai take jin dadin Hira da shi, mutun ne mai fara'a da barkwanci gashi yana Biye ma duk abunda Innani ta zo da shi baya kusheta Shiyasa da ta gansa ta rasa ina zata sakashi Saboda Murna. Kamar an bude famfo haka ta shiga labarta masa abunda ya kawosa, har da sauran Labaran da bai sani ba na game da Hasiya. Kai Tsaye mallam Zakari ya kalli Innani kafin yace"Naga matar jiya tare da ita ya biya wajena, yace Zariya zai kwana yau tun safe zai kama hanyar Abuja" Sai Innani ta rike baki ta kasa mgana, Shigowar Umma da Abba ya hanata wata mgana. Umma ta duka zata gaishe shi ya daga mata hannu da sauri yana fadin"mike kawai abunki salamatu yau bazan karbi gaisuwarki ba, sai kin gayamin babban Dalilin ki na kin sakama auran da Abubakar ya yi albarka? Ke shad'aniya ce da ki ke ja da Hukuncin Ubangiji salamatu.? Yadda ya ke fad'an ne yasa Umma durkushewa a gabansa cikin rawan murya tace"Baba ka tsaya ka Saurareni." Cikin daga murya yace"To ina sauraranki, fad'i abunda ke bakin ki." Gatse ya yi mata ammh bata gane ba cikin Rawan baki ta fara fad'in"Baba yaron nan fa aure yaje ya yi a Boye bamu sani ba? Kai Tsaye yace"Shine mene? Kallonsa ta yi cikin mamaki bakinta na Furta"Baba.! "Nace shine menene don ya yi aure baki sani ba, sai daga baya kika sani? Sai Umma ta maida kanta kasa ta riga daman tasan mahaifin nata bayan Sadiq zai bi. Cikin fad'a Mallam zakari ya cigaba da fadin"Ke Sakarcin ki bai baki yakamata ma ki godema Allah ba, in da ace yau matar bariki ya samu fa ko da kin ji Labari kina da yarda zaki yi ne? Ko kuma ace cikin da ke jikin Matar ba ta hanyar aure ya same shi ba? Sai ki ce kuma mene a wannan Lokacin Salamatu? Ya fad'a yana kureta da ido Umma sai kuka Innaani na gefe tace"Haka ma Sulaimanu yace min da zai min nasiha shiyasa na yi shu da bakina.". Mallam zakari ya kalli Innani ya na fad'in"Ke ma ai naga laifin ki Tsohuwa, kema ai uwa ce ga salamatu har da shi Sulaiman din, in suka yi ba daidai ki had'a su ki yi musu Hukunci, ammh sai ki barta ta na azabartar da yaro kan hanyar gaskiyarsa, kuma ma abun haushin duk kuna zaune kuna kallonta yanzu ba domin yaron nan ya yi Hankalin zuwa ya gayamin ba. Da sai abu ya kwabe ya lalace sannan zan sani." Innani na jin haka kawai sai ta saka kuka har da Cire gilashi ta na fad"in"Ni ina ruwana, mi ye nawa? Na zabi yin shuru ne tunda abu na tsakanin bare da na gida, in na saka baki a kan lamarin sultana sai Magajin gida yace ina ja da Hukuncin Ubangiji in kuma na saka baki na goyo bayansa sai ace naki na gida na Fifita bare, in kuma na yi shuru da bakina shima bazan tsira ba." Kawai sai ta fara jan Hanci ta na cigaba da fadin"Kuma salamatu naga ranta ya baci, kuma tsakani ga Allah d'anta ne kada na cika saka baki taga kamar zan nuna mata iyakarta ne, sannan shi kanshi Sulaimanu bata ji mganarsa ba ballatani, ni a suwa? danwake ya shiga hotel ai bazata ji mgana na ba, shiyasa na koma gefe na yi Shuu da bakina kaji dai dalilina ni kam a daina ganin laifina." Ta karishe fad'a ta na share Hawaye da Haban zaninta. Malam zakari yace"To shikenan ni yanzu zan ci Mutumcinta, in ku ta raina ku ni bata isa tace zata kawo min wargi ba. Bar ganin kin tara ya'ya da jikoki sai na kwade'ki anan wajen Tunda sakara kike kin girma da tunanin da ko yaran ki na tabbata ba zasu aikata abunda kike aikatawa yanzu ba." Umma dai ba baki sai shesheshekan kuka ta ke yi gwanin ban Tausayi ita tana gani ta na kan gaskiyarta an ki sauraranta Mallam zakari kuwa Abba ya shiga yima fad'an me yasa ya Biye ma Umma ta na wannan Shirmen. Abba ya gyara zama yana fadin"Na yi mata uzirin sanin halinta, na barta ta nuna Fushinta tunda ita uwace ammh ban dauka abun nata zai zarce zatona da Tunanina ba." Mallam zakari yace"Ai kaji inda aka samu matsala, ai su mata ba'a kyalesu ace za'a ga iya gudun ruwansu wlh kana zaune sake da baki sai su wuce Tunaninka  kamata ya yi tun farko ka tka mata Burki ka nuna mata kai ne sama da ita ba ka zauna ka saka mata ido ta na abunda taga dama ba." Abba dai sai ya fara ban Hakuri, mallam Zakari kuma sai ya koma kan Umma ya na ta yi mata fad'a ta inda ya ke shiga bata nan ya ke fita ba. Fad'i ya ke yi"Ke bazaki godema Allah ba, Allah ya baki duka yara natsassu, ba wani mara ji a cikin su, menene abun damuwa saboda ya  yi aure baki sani ba? Naji bai kyauta ba Boyemun ku da ya yi, ammh kuma da kika sani me ya kamata ki yi? Ba sai ki godema Allah tunda auran ya yi ba, ki zauna da Danki ku fahimci juna ammh sai ki zauna kina wani shanshanci wai har kece kike fad'in wai sai dai ya zaba Tsakanin ita yar wajen naki da ita matar nasa? An ya salamatu kina da aldaci kuwa a Rayuwaarki? Kuma kina son ki gama da Duniya lafiya kuwa? Sai Umma ta kara karfin kukanta cikin rawan murya tace"Baba baka san irin yarinyar da ya aura ba ne shiyasa ka ke goyama yaron nan baya." Mallam Zakari yace"Bansanta ba, kaji min wata mgana jiya nan suna gidana na ganta har mun yi mgana da ita yarinya karama miye laifinta? Sannan ta na Dauke da ciki abun Tausayi ko ta haka bazaki tausayamata ba, tunda ai kema uwace kinsan komai." Umma tace"Baaba Matar fa an ce fa farar kafa gareta sannan bakar Annoba ce, shi kanshi Sadiq din ya sani duk wanda ta aura ko ya rasa lafiya ko Dukiya ko rai to Baba wannan matar abar so ce? Ai in nace ya saketa ban yi laifi ba." Mallam Zakari ya yi shuru ya na kallon Umma cikin mamaki kafin ya kad'a kai yana fadin"Eh na shaida ba shhakka, ashe duk ilimin da na baki kin yi watsi da shi, a wani Nafsin akace akwai farar kafa a musulunci? Sannan ita Allah ce da zata Talauta mutum ko ta kashesa! Kaji wani banzan Tunani wajen salamatu Tunani irin na Jahilan farko da ba su san addini ba" Ya fad'a cikin takaici Abba na gefe yace"Shi na gani, to Ubangiji shine fa komai, ta yaya don wani abu ya Faru da wani sai ace kuma wani ne ya yi masa  kaga ai an kauce ma sanin Allah ta wannan bangaran" Cikin fad'a ya karb'e da fadin"Tuni ma an kauce ma Fad'in Allah da Monzonsa sannan Tauhidi ya yi Targad'a, babu iklasi kwata kwata a al'amarim salamatu." Umma na sharan hawaye tace"Baba kuma fa bazawara ce, auranta Biyu kuma an ce duka mazajen sai da ta nakasu sannan ta rabu da su, ina zan saka kaina in na rasa Sadiq shi kad'ai gareni namiji kwara d'aya tak shiyasa nake yin wannan abubuwan saboda kare lafiyarsa." Mallam Zakari ya katseta da Fad'in"Kafin ki samu Sadiq din a baya kin san zaki same shi? Nace kin san zaki same shi? Umma sai ta girgiza kai cikin fad'a ya cigaba da cewa"Baki san zaki same shi ba Allah ya baki shi, to kin isa ki hanashi ya kwace shi Lokacin da ya ga dama ne? Kuma da kike fadin kina yin wannan abun ne saboda kare lafiyarsa wacece ke da zaki iya kare lafiyarsa, ko daman chan ke kike Tsare da lafiyar tasa? Salamatu kina wani abu kamar mara ilimi Allah ne kad'ai ke tsare da bayinsa ba wayon mu ba, kuma ba Dubaran mu ba ke baki isa ki zama kariya ga Rayuwar Abubakar ba Tunda ba tare kike yawo da shi ko da yaushe ba  kuma da kike wani izgilanci fad'in bazawara to sai me? Su zawarawa ba Mutane ne ba ne? Ko su ba su da rai ne? Ki shiga Hankalin ki fa, ke da kike ganin kanki a gidan mijin ai baki wuce a yanzu ki zama bazawarar ba" Da Sauri Umma ta Dago ta na kallonsa Lokaci daya ta na nuna kanta da fad'in"Ni kuma Baba? Kai Tsaye yace"Eh ke fa, kin wuce  ki zama bazawar ce? Kuma kada ki manta ke uwace kina da ya'ya mata Rututu suma acikin su baza su wuce kaddaran haka ta faru da su ba sai naga yadda zaki yi, tunda zawara ne su, bazasu kara auruwa ba." Umma sai ta kara saka kuka Mallam Zakari kuwa bai barta ba sai da ta yi masa alkwarin taji kuma In sha Allahu zata gyara. Ba zata kara cewa ya zabi daya daga cikin matansa ba, sannan zata cire bakinta a sha'anin matan Abubakar in kuma ya kara ji to ranta sai yafi haka baci. Umma bata da mafita sai ban hakuri ganin yadda ya Dauki zafi. Suna zaune yana kara yi ma ta nasiha ganin ya dauki zafi da farko yanzu kuma sai ya koma nasiha da lallashi. A lokacin a ka kira Abba a waya daga chan Abuja ma'aikatar Da Sadiq ke aiki. Tunda Lokacin da mutane suka kawo agaji a wajen da akayi hatsarin an samu dai an cirosa daga motar sai dai wayarsa ta fashe, ta cikin motar aka ga I.d card dinsa na wajen aiki sai wani jami'a cikin  jami'ai masu kiyaye had'ura na titina Road Safey da suka zo wajen ya dauki lambarsu ya Kira su ya gayamasu bayan ya yi musu bayanin sunan ma'aikacin nasu. Su kuma daman suna da duka bayanan ma'aikatan su kuma bayan Lambarka kana saka wata lambar ko na mahaifi ko mahaifiya anan suka samu lambar Abba suka kirashi suka sanar da shi abunda da ke faruwa, sannan suka ce za su Turamai lambar jami'in da ya kira su. Kawai gani suka yi Abba ya mike yana ta jera Uban salati. Da Sauri Umma da mallam Zakari suka mike suna tambayan lafiya? Innani kuma har ta fara gyangyd'i kamar daga Sama taji Abba na fad'in"Abubakar ne wai ya samu Had'arin  mota yanzu daga ma'aikatarsu ta chan Abuja suka kirani suna fad'amin." Sai ga innani ta fado daga kan kujera ta na fadin"Na shiga uku ni Dije, wani Abubakar din ba dai magajin gida ba? Umma kuwa kasa ta koma ta zauna Dabas ta Dora hannu a saman kai ta na fadin"Shikenan abunda na ke gudu ya faru, na shiga uku na lalace wayyo d'ana." Mallam Zakari kuwa salati ya saka yana tambayar Abba a ina abun ya faru? Abba yace ba su yi masa wani karin bayani ba ammh sun ce za su turo masa lambar jami'in da ya Kirasu sai ya kira yaji a ina ne? Kuma sannan a wani Halin Sadiq din ke ciki. Abba jikinsa na rawa ana Turo lambar ya latsa kira bayan bayanin shi mahaifin Abubakar ne wanda ya yi hatsari yanzu aka kirasa daga ma'aikatarsu na Abuja kuma su suka Tura masa lambarsa. Jami'in yace"Hatsarin ya faru a tsakanin barin kaduna ne zuwa Abuja, kuma mara lafiyan yana asibitin Sojoji na 44 da ke kaduna za su iya zuwa domin ganin Halin da ya ke ciki." Abba da mallam Zakari ko Tsayawa jin ta ihun su Innani ba su yi ba suna fita Direba daman yazo ya na jiran Abba za su fita kawai suka fad'a mota Hankali tashe. Sai bayan fitarsu ne Umma ta fito ta na kuka ta yi shashen Mama ta na fad'a mata abunda ke Faruwa. Mama ta Rude' fad'i ta ke yi"Mun shiga uku, a ina abun ya faru? Umma na kuka tace"Bansani ba, Abban siyama da Baba da yazo da Safe sun fita ba su yi mana wani bayani ba." Mama itama sai hawaye hankula suka tashi ita Sultana ihun Innani ne ma ya fito da ita a haraban gida ta na kuka da jiniya ta na fad'in"Bala'i da Annoba sun sauka a rayuwar magajin gida." Siyama ke gayamata ta na kuka cewa Yaya Sadiq ne ya yi hatsari. Itama nan da nan ta rud'e daman kuma ta gama kukan fad'an babanta kenan sai kuma ga wani bakin Labari. Kafin wani Lokaci gabadaya wannan Ahali na nesa da na kusa sun san abunda ke faruwa yan kusa kuwa irin su Surayya, Sadiya, Sajida Sa'ima, sakeena, Sa'adatu duk sun hallara na nesa kuwa irin su Saddiqa da su saliha sai faman kira suke suna tambayan yadda ake ciki. Abba kuma yace suna hanya har Lokacin ba su isa kaduna ba. Hankali sun tashi, Innani kuka ta dinga yi ta na fadin in Magajin gida babu shi ne gwara su fad'a mata ta san gaskiyan mgana. Umma kuwa har sai da idanuwanta suka sauya muryanta ya dishe, Surayya ma ta yi kuka kamar mene, sai dai ita ke ta faman waya da su Abba tana ce musu suma ga su nan za su taso ammh kuma Abba ya hana yace su dakata su fara isa su ga Halin da ya ke ciki. Sultana kamar mai aljanu sai shidewa ta ke yi, kawai ta na Tuna rashin kunyar da ta yi masa ne ranar kafin tafiyarsa. Su sajida kuwa ko duba Halin da ke ciki ba su yi ba fad'i suke yi shikenan Sadiq ya Dauko abunda zai kashe shi ba karya komai ya Faru da shi silar wannan bakar Annoban da ya kwaso musu ne. Umma dai sai kuka bata mgana su Baba sammani ma Tuni sun samu Labari dagachan suma suka ce za su wuce kadunan domin su ga Halin da ke aciki. Abba sun isa kaduna wajen uku na rana ne, shima domin Direba ya yi gudu ne sosai suna zuwa asibitin 44 shashen Emergency suka nufa Tunda suna ta waya da wannan jami'in yace tare da shi aka kawo Sadiq asibitin shi yaje ya Dauko yan Sanda Tunda cases ne na hadari sai da jami'an Tsaro zasu karbesa. Sun je sun iske har alokacin Sadiq na Emergency, sai dai yana nan a raye ammh kuma ya samu Raunika, akwai karaya a hannunsa na dama sai kuma karaya a kafar dama sai kuma Raunin da ya samu a kansa da gefen fuskarsa sai kananun Rauninka a sassan jikimsa. An gode Allah ma tunda ya farfado sai dai baya cikin hayyacinsa sannan sunce Hoton kansa za su yi zuwa Gobe su gani ko Buguwar ta tab'a cikin kansa. Abba da mallam Zakari sun shiga sun gansa sai ga Sadiq halitta duk ta sauya kansa duk ya kumbura. Abba ma sharan hawaye Mallam Zakari na sharan hawaye. Jami'in shi ya ba su kayan Sadiq da suka samu a motar wayarsa da I.D card ,key din mota sai Wallet d'insa mai Dauke da kudi da Atm din bankunansa sai wasu Takardu. Allah yasa an yi saurin adanasu da tuni an nemesu an rasa. Suka rabu da  su Abba  suna yi masa Godiya bayan Abba ya yi masa ihisani. Shi ya gayamusu ba Motar ta da gogesa kawai motar ce ta kwace masa, kuma in da Abun ya takaita ba wata mota mai zuwa a gaba da abun yafi haka Muni. Abba bai san yana iya kuka ba sai da yaga Sadiq cikin wannan Halin, shiyasa ko da Surayya ta kara kira ya kwantar musu da Hankalin cewa Sadiq na raye kuma jikinsa da Sauki shi yace kada su taho su bari sai gobe ko Jibi. Su Baba Sammani ne Tunda sun taso bai hanasu zuwa ba, suma sai yamma suka iso Abba me ke ta shiga yana Fita zuwa Lokacin har Alhaji Jibril da Mubarak da salima suna asibitin, salima ta yi kuka kamar ranta zai fita , tunda su ke ba su taba ganin tashin hankali irin shi ba, duk wanda yaga Sadiq a wannan Halin sai ya Zubar masa da kwallah shi Abba ya sakaya abun, ammh Salima da suka yi mgana da Big sis ta na kuka tana gayamusu halin da dan'uwansu ke ciki, tace ma yanzu a daran nan Hoto kansa za'a yi masa tunda ya samu Buguwa a gani ko buguwar bai shafi kansa ba. Sai gida ya kara rikicewa, da koke koke duka ba wacce ta yi shirin komawa gida nan suka kwana da kuma Shirin gobe da safe za su bi bayansu Abba suma su ga halin da Dan'uwansu ke ciki. Tahir ma a daran Surayya ta kirasa ta na gayamasa abunda ke faruwa ya Rud'e daman kuma yana katsina ne yace gobe zai biyo motar asuba zuwa kaduna in sha Allahu. Mallam Zakari da su Baba Saminu har Abba ma a gidan Alhaji Jibril suka kwana tunda su a tsarin asibitin ba'a kwana da majinyaci sai dai gobe da Safe mutum ya dawo, kuma yana cikin Emergency har Lokacin ba'a Fito da shi ba an samu dai an yi masa Hoton kan sakamakon ne sai a washegarin zai fito. Alhaji Jibril fadi yake yi"Sai da  daman nace, yarinyaar nan auranta ba alheri ba ne, gashi ta saka yaron nan cikin jarabawa." Su Abba dai suna ta Sadiq ba su ko Biyema Alhaji Jibril da manganunsa ba. Dagachan Gusai ba su yarda sun gayama su Abba suna tafe ba, Mijin Surayya ya dauketa ita da su Umma da Mama da Innani sauran kuma mijin Sa'ima ya Tuka su, sai kuma Direban mijin Sadiya shima ya ba su mota dai uku duka kuma gidan suka tafi, megadi kawai aka bari mallam Taju ya na binsu da Fatan isa lafiya da kuma Allah ya tashi kafad'un magajin gida. Da azahar suka isa can suka iske Tahir ya iso shima Tun safe sai dai sun samu hankula sun kwanta Tunda sakamakon Hoton kai ya fito kuma komai Normal buguwar ba ta shafi kwakwalwar kansa ba. Kuma an fito da shi daga Emergency zuwa daki na musamman Cuwukan ne kad'ai suka samu Dressing ammh karayan ba'a Daura shi ba Abba suna ta shawaran in da za'a bar shi ko anan din ko kuma a kaisa asibitin dala kano a yi masa Daurin asibiti. Har alokacin Sadiq barci ya ke yi a wahale sai dai ance da safe ya farka yana ta kukan kansa. Dukkansu matan nan da kuka suke Fitowa daga dakin nan Sultana kam ta kasa shiga ma saboda tashin Hankali a ranar ma sai ga su mallam Shitu da su Goggo Hassu sun zo suma cikin Tashin hankali. Saboda yanayin Tsamin jikin Sadiq yasa mallam Zakari yace a barsa anan a yi masa Daurin asibiti ammh in fa akace za'a rika Kai can da mara lafiya nan za'a iya samun matsala. Domin shi Baba Sammani yace gwara a yi Daurin gida zai fi yin kyau..mallam zakari yace halin da yake ciki za'a duba. Karshenta dai aka tsaya a matsayar anan kaduna zai zauna a yi masa Dorin asibiti a gani, kuma Abba na saka hannu ya bama likoticin dama sukace a daran za su daura shi. Abba bai bar su Umma ba saboda Innani Tunda suka zo ta ke faman koke koke, daga  asibitin gidan Alhaji jibril suka tafi sallah dagachan kuma yace su kama hanyar Gusau inda ma yaji dad'in ganin mazajen su Surayya sai ya samu salaman cewa zasu kula da iyalansa. Maallam Zakari ma Abba ya yi ya koma gida yace yana nan sai yaga yadda Jikin Sadiq ya yi. Tahir ma da ya yi zuru zuru yace yana nan sai zuwa gobe ko Jibi zai koma ganin haka yasa su Baba Sammani suka juya zuwa shinkafi su da su Goggo Husai a ranar. Ita Surayya ba ta bi su Umma gidan Salima ba, ta  tsaya a asibitin tace anan zata yi sallah abinci kuma bazata ci ba, suna ta waya da subai ne da ta taso daga kano Saddiqa kuma gobe zata taso daga Kebbi gabadaya hankulansu yaki kwanciya, Shahida ma ta iso daga katsina dazu kowa ka gani Fuska ta jeme sai jan ido kawai. Shiyasa bata san abunda ya faru ba, ashe suna fita daga asibitin nan Umma ta bama Sadiya da Sajida kudin mota tace suje Zariya su fattaki Hasiya daga Rayuwar Sadiq su tabbatar da bata kara marmarin kusanto Rayuwarsa ba. Mama ce kara zuga Umma tana fadin ai wannan yarinya ba matar zama ba ce Annoba ce Tunda Sajida tasan gidan ita tayi musu jagora Umma tace su yi sauri zata san yadda tayi suka b'ata Lokaci kuma Surayya bata fahimci komai ba. Ko tasha ba su je ba, a bakin hanya suka samu mota duk da Tsadar da aka yi musu suka shiga hakanan sai Zariya. ********** Zariya. Tun ranar da Assadiq ya bar ni zuwa Abuja na ke ta kiran wayarsa a kashe, har washegari to ban damu ba sai na yi Tunanin kila babu chaji ne. Ko aiki ya yi masa yawa zai kirani Daga baya, ban kara shiga damuwa ba sai da naga har dare bai neme ni ba, kuma na kara kiransa har Lokacin wayarsa a kashe. Ranar barci na rabi da rabi ne, sai kuma da safe na tashi da sanyin jiki da faduwar gaba. Haka kurun nake jin wani iri acikin jikina. Ranar na kira wayar Assadiq ban san adadi ba, in nace bari na kira Anty Surayya sai na kasa sai nake ganin kamar zata ce na cika zakewa ne shiyasa na kasa kiranta. sai dai na kasa natsuwa ina ji araina da wani abu ni bai saba min haka ba, abunda bai taba Faruwa ba. In dai Assadiq ya tafi Abuja yana isa zai kirani ko ya yi min sakon cewa ya isa lafiya ammh yau har an kwana Biyu ban ji daga garesa ba. Daman na bari ne zuwa dare in ban same sa ba daga baya zan kira Anty surayya naji ko ita sun yi waya da shi. Allah sarki bansan abunda ke faruwa ba, ita kanta Surayya tashin Hankalin da ta ke ciki ne yasa ta manta da Hasiyar kwata kwata ballatana ta kirani ta fad'amin. Tun safe ina kwance kamar ruwa ban iya yin komai ba abinci ma Maman suhailat ta aiko min da Doya da miya naci na sha ruwa dakina kaca kaca cikina ya yi nauyin da yanzu ban iya moruwa. sai dai na kwana in an kira sallah na tashi nayi gabadaya hankalina baya jikina. Wajen biyu da wani abu na rana naji ana bugamin kofar d'aki kamar hauka abunda ya bani tsoro shine jin ana ta mganganu kuma naji muryan Maman Suhailat na kiran sunana. Sai na Rarumi dankwalina na taka da Cikina a gaba naje na Bude kofar sai dai me? Ko gama Bude kofar ban yi ba aka Bugo min kofar saman cikina sai gani na yi baya na fad'i a kasa Dabas. Ni dai ina ji Maman suhalat na salati kuma naga sanda yan'uwan Assadiq suka tsallake suka shigo dakin suna fadin"Bakar Annoba zo ki fice daga Rayuwarmu mun gode, ammh bazamu bari ki karisa mana Dan'uwa ba." Maman suhailat ita ta kamani ma mike ina raba ido, Sajida ce tsaye a gabana ta nuna ni da yatsa tana fadin"Ki kwashe kayanki kaf ki bani key din dakin nan zan Rufe dakin zaman ki da Dan'uwan mu ya kare, tunda burin ki ya cika kin kusa kashe  shi." Sai Hankalina ya tashi cikim Rawan murya nace"Me ya faru da Assadiq din? Kusan ni da maman suhailat muka yi tambayan a lokaci d'aya. Ban tsamnani ba sai da naji Sajida ta kwasheni da mari sai da na fad'a jikin Maman su Suhalait saboda azaba. Ta kuma nuna ni da yatsa tana fadin"Har ki ke da bakin tambayata? To yana chan a gadon asibiti ya karareaye duk kuma saboda ke bakar Annoba da Jaraba, Saboda haka Umma tace mu zo mu sallame ki, ki kara gaba ki yi nesa da Rayuwar Dan'uwanmu in ba haka ba ke zaki rasa taki rayuwar." Hankalina ya tashi cikin Firgici na fashe da kuka na kasa mgana. Maman suhailat ce ke fadin"subhanallah ku tausaya mata baku ga halin da ta ke ciki ba ne? Sadiya tace"Mu kuma baki ga Halin data sakamu ba ne? Daga wajenta ya ke ya samu hatsari ya na chan baisan inda kansa ya ke ba, kuma kice mu kyaleta wlh sai ta kara gaba malama ki zo ki kwashi kayanki ko mu yi miki watsi da shi.'" Ni ban damu da kaina ba irin Assadiq da akace yana chan baisan inda kansa ya ke ciki ba. Duk da halin da nike ciki haka na Duka ina rokon su gayamin inda Assadiq ya ke su kuma barni naje na gansa daga baya sai na tafi ammh sukace ban isa ba. Ganin zasu faramin watsi da kaya yasa Maman suhailat tace na bar kuka na shiga na had'a kayana su Sajida ba su da Mutumci. Ina kuka harda majina na had'a kayana akwati biyu Maman suhailat na tayani, su kuma suna Tsaye zagi da cin Mutimci sai wanda suka manta. ni kuma ina ta Rokon su, su barni naje na Duba Halin da Assadiq yake ciki sukace ban isa ba. Kaya kawai suka bari na Dauka na Dauko wayata suka kwace da jakata suka caje komai suka kwashe kudin ciki har da Atm dina, Hijabi kad'ai suka barni na saka suka Turoni waje suka rufe dakin su kuma saka key din a jaka. Allah yasa gidan dagani sai maman suhailat, itace ke ta ba su hakuri ba su ma tsaya sauraranta ba suka min kashedin ko da wasa kada na kuskura na kara nuna ma san kaninsu, na jira a duk inda na ke zan samu takardan sakina, mari da dunguri ba wanda ban sha shi ba suka tafi da komai suka barni Durkushe ina ta kuka. Maman suhailat tajani dakinta ta na ta lallashina da bani baki. Taso ma na kwana a wajenta kafin da safe asan mafita nace mata ta bani kudi zan tafi, sai dai ban nuna mata in da zuciyata ke rayamin naje ba. Sai nace mata gidan Adda Fati zan tafi kamar ta sani sai ta bani 5k ta kuma rakani har bakin Titi na samu adaidaita. Sai da muka d'au hanya sannan nace ya kaini tasha, motar gada zan hau gwara naje wajen Amma. Da naje na sauke ma Adda Fati halin da nike ciki gwara na tafi wajen uwata a wannan Halin da nike ciki lallashinta na ke Bukata. Ina mota ina kuka kukan tunanin wani Hali Assadiq ke ciki, shi kawai nake Tunani a raina kuwa ina ta masa addu'an Allh ya bashi lafiya Allah Sarki ashe Shiyasa najisa shuru ashe ashe shi ga halin da ya ke ciki ban sani ba. A cikin raina na yanke shawaran zan rabu da Assadiq ko saboda son da na ke yi masa na barsa ya yi rayuwarsa cikin salama sannan na kara aminta da maaganar mutane a kaina ni din Bakar Annoba ce. Gwara na je na zauna gaban Amma na haifi abunda ke cikina na Reneshi in Assadiq ya barmin shi ya Rayu dani in kuma bai barmun shi ba shikenan sai na zauna na cigaba da bautar Ubangiji har ta Allah ta kasance. Ammh na hakura da yin aure na daina jazama mutanen da suka min hallaci wahala a rayuwarsu. Na isa gada bayan mangariba saboda motar Bus ce, sai dai a halin da na iske Amma aciki bazata iya ma fahimtar nawa Halin ba. Na iske Adda kwance ba lafiya sosai kuma taki yarda a kaita asibiti, a sanda na isa jikinta ya yi zafi ya'yanta duk suna kanta tare da Amma shiyasa ba wanda ya iya Fahimtar ina cikin wani hali, ni ma ai sai na Boye nawa na koma cikin yan jajantawa. Amma kuma ba ta cikin natsuwarta a tunaninta na zo ganinta ne ta ma manta cewa Tsohon ciki gareni haihuwa ko yau ko gobe. Na isa Garin ko awa daya ban yi ba Adda ta amsa kiran Ubangijinta. Innalillahi wa'inna ilaihirraju'un Kullu nafsin za'ikatul maut." Kowani rai sai ya dan'd'ani dacin mutuwa. Sai gani ina taya Amma kukan Rashin yar'uwata a raina ina gayama kaina na Dunkule damuwata kada na bari Amma taji, in ba so na ke a yi gawa Biyu ba tun adaran na dauki wayar Amma na kira su Adda Fati na gayamusu. Suma ta mamakin zuwana su a tunaninsa ko naji tashin jikin Adda ne yasa na tafi ba su san rashin dad'i ne ya kawoni ba. Har Ramatu sai da na kira da wayar Amma na gayamata tace zata biyo su Adda Gobe da safe. Haka ko akayi sun iso har da Inna Talatu sun kuma iske har an kai Adda Gidanta na gaskiyaa. Ya'yanta na ta kuka damu kanmu Sabida mun yi rashi, Amma tafi kowa jin mutuwar nan saboda Adda ce kadai yar'uwan data rage mata Cikim Dangi. Allah Sarki Rayuwa Allah ai baya barin wani domin wani yaji dad'i. *Janafty* *TMWBK3011* *TMW is a paid Novel, Pay 500 for regular or VIP N1K, Via 0552179550 Jamila Umar Gt bank, 09069067488* https://chat.whatsapp.com/K3rO5UonX4GDVxtQbA5mZl PAID ADVERT✅ Assalamualaikum wa rahmatullahi ta'ala wa barakatuhu!!! Wannan group din dai na komai da komai ne. A taiqaice *Farashin mu na daban ne compared to sauran Yan kasuwa *Kaya masu kyau da quality. Abinda kika zaba shi za a Baki * Swift delivery.watau waybill a sauqaqe da Yardar Allah * Muna sake New Arrivals ka fin su cika Gari * Muna iya duba maku kaya a good price ko da ba namu ba ne idan kuka Aiko da hoton kayan Allah sa mu qaru da juna Ameen Babu wanda ya lura da Halin da ni ke ciki sai ranar da aka yi addu'ar uku na Adda, sannan ne Adda Fati ta Fahimci ko sau d'aya bata ganni da wayata ba shine ta ke tambaya ta. Ni kuma cikin sauri na sanar da ita cewa ta lalace na barta a gida ne. Daganan bata kara tambayata wani abu ba, a ranar Ramatu da Inna talatu suka tafi tare da yan dogon gida na samaru maman boy da maman Salihi sun zo Amma gaisuwa a ranar, sai suka koma tare da su Ramatu. Adda Rukayya ma sai da ta kara tambayata ina wayata nace ta lalace na baro ta gida, ita dai cikin mamaki tace"To da wata waya ku ke mgana da Abubakar din? Mirmishin yake na yi mata kafin nace"ai baya garin, ma'aikatan su ta tura su aikin titi wani gari in da ba Service shiyasa ma yace nazo nan wajen Amma kafin ya dawo." Saboda tun washegarin Biyu da Rasuwar Adda na saci wayar Amma ina ta kiran wayar Assadiq ammh yaren guda d'aya ne wayarsa ta na kashe ne. A dangin Babanmu Baaba ta lagos ce kad'ai ta kira Wayar Amma ta yi mata gaisuwa tace itama Baba Saminu ke gayamata ki rasa ta ina suke samun Labarin mu. Shi ko gaisuwan bai kira ya yi ma Amma ba ammh ya iya yad'a ma wasu. Tare muka zauna da Amma har aka yi addu'ar bakwai din Adda, ba na yarda na yi kukana gaban yan'uwana Saboda ba na so su fahimci yadda Rayuwata ta kara yin tsudum a cikin tsaka mai wuya. Kuma ko da sun ga idanuwana sun kumbura ba su cika damuwa ba, a tunanin ina kukan wannan rasuwar da aka kwantsama mana ne. A daran da Adda ta yi bakwai ya'yanta suka taramu har da Amma suna rokon mu kada mu ce zamu dauke Amma ta koma wajen mu da zama, bayan Adda ba su da wata uwa da ta wuce Amma saboda haka zata cigaba da zama tare da Hamma Isuhu da iyalansa. Mu ma daman bamu da wannan niyar ballatana Amma bazata taba aminewa da komawa zariya ba, nan take tace ba inda zataje tana tare da su itama har mutuwarta tazo ta isketa nan da nan sai kuka sai mutuwar ta dawo sabuwa. Allah sarki ashe mutuwa bata  daukan wanda ke ciwo haka na raya a raina, Amma ce lafai lafai Adda kuma macece mai kazar kazar da alamun karfi Allah dai ya jikanta da Rahma. Washegari kwana takwas su Adda Fati suka fara Shirin tafiya abunda ya basu mamaki ganina kwance bana shirin tafiya. Habiba ce ta kalleni ina kwance da katon cikina a gabana tana fad'in"Adda Hasiya ke bazaki tafi ba ne?  naga baki shirya ba ne? Duk kuma sai da ta yi mgana suka maida hankalinsu kaina har da Amma da ke zaune a gefena. Adda Rukayya tace"Ina zucci zuccin na yi mgana kika rigani, Hasi nan zamu barki ne? Ina kokarin tashi zaune nace"Eh yace in ya dawo zai zo ya daukeni." Sai ba su damu ba sukace Allah ya kaimu ai bakomai sai na kara taya Amma zama Tunda har lokacin bata wani saki jikinta ba. Amma ta kallo inda jerin akwatunan kayana suke cikin mamaki tace"To zai dad'e ne shi megida naki haka? Naga kin kwaso kaya har akwatina Biyu? Gabana ya fad'i ammh kuma sai na yi saurin Washe bakina zan yi mgana. Ammh sai Adda Fati ta rigani da fadin" Amma kika sani ko kayan haihuwa ne, tunda Adda bata raye ke zaki zama uwar zoman Hasiya." Amma mirmishi kawai ta yi kafin tace"Allah ya jikanAdda, ko a satin da zata rasu sai da tace min Hasiya ta shiga watan haihuwanta ko? Hasiya na ranta ta yi alkwarin zuwa ta zauna dake ta kula da ke tare da abunda kika haifa ashe Allah mai Hikima bazai bata damar ganin wannan Lokacin ba." Gabad'ayanmu muka had'a baki wajen fadin"Allah ya jikanta da Rahma." Amma ta amsa da Ameem Ameen ta na sharan kwallah. A ranar su Adda Fati da Adda Rukayya tare da Habiba suka koma Zariya suka barni tare da Amma ina sake lallashinta sannan ganina yana sawa tana sakin jikinta. Ya'yan Adda suma kowa ya koma wajen neman abincinsa mai auran ma mace itama ta koma gidan mijinta daman Badd'o na wajenta tun Adda na raye yanzu ma wajenta ta koma. Sannan har a lokacin makota da abokan arzuka suna ta shigowa kara yi ma su Amma gaisuwa. Ni kuma koda yaushe tunanina wani Hali Assadiq ya ke ciki?. Har yau da Adda ke cika kwana goma da Rasuwa na kara gwada layinsa ammh amsar dai iri d'ayace a kashe. Sai na fara tunanin ko dai wani mummunan abu ya faru da Assadiq ne? Kuma ni sun kwace wayata ballatana na samu lambar Anty Surayya na kirata naji wani Hali yake ciki, a koda yaushe ba na iya barci balle ma Tunda cikina ya tsufa ban cika samun  barci ballatana ni da na ke cikin Damuwa da halin kakani k'ani. Ko alama ban yarda na bari Amma ta Fahimci wani abu ba, ina son uwata shiyasa ba na fatan ni nayi sanadiyar gayamata abunda zai kara Ruguzata shiyasa na yi shuru da bakina sai dai ina ta addu'an a duk inda Assadiq ya ke Allah ya bashi lafiya ya tada kafad'unsa ni ma kuma Allah ya sauke ni lafiya cikin ikonsa da kudurarsa. ******** Assadiq ya dawo hayyacinsa tun kwana hu'du da faruwar Lamarin, kuma Alhamdulillah an yi Daurin kuma ga dukkam alamu akwai alamun nasara a aikin. Kuma ba shi da kyamar jiki, da sauri Cuwukan jikinsa suka dauko hanyar warkewa har kumburin kansa ya ragu sai abunda ba'a rasa ba. Abba ya koma gida sai dai yana zuwa ganin Assadiq bayan kwana daya ko Biyu Auwalu ne yaron Baba Saminu ke tare da Assadiq a asibitin sai Tahir da kan zo shima Lokaci bayan Lokaci. Hidimar su kuma gabadaya ta na kan Alhaji Jibril ne, Salima kuma ke kawo  abincin safe da yamma da rana ne in tana makaranta Hajiya Murjanatu ke bama direba ya kawo musu anan cikin asibitin. Kaf yan'uwansa mata ba wacce bata zo ta gansa ba, kuma ganin har ya dawo hayyacinsa yasa wad'anda ba yan garin ba suka koma gidajensu da wuri sai dai kullum suna cikin kiran wayar Auwalu domim tambayar lafiya dan'uwansa Tunda shi ba waya a hannunsa. Innani dai sau d'aya Abba ya sake Dawowa da ita ta gansa  ganinsa ido Biyu har suna mgana yasa hamkalinta ya kwanta ta daina damun mutane da kuka achan gida, Umma ma kamar ba ita ba, duk sai ta rame Abunda ya faru da Sadiq ya dimauta ta matuka, sai dai zukata sun kwanta tunda suna ganin Sauki sosai sai Hamdala. Baki yan'uwa da mutanen arziki sun ta tururuwan zuwa kaduna Duba jikin Assadiq kaf mutanen shinkafi har da makota sai da suka zo kaduna Duba Assadiq daga gusai ma yan uwan Mama da mazajen yan'uwansa mata tare da Dangin Umma daga Gummi suma mota guda suka zo duba jikin nasa, kowa kuma ya koma da salama ganin har mgana Sadiq din nayi sannan yana gane wanda ke tare dashi. Har Hajja kakar Tahir sai da tazo ta Dubashi tare suka zo da Tahir sai yayansa Kasim, nan suka barshi ya kwana su kuma suka koma aranar, Sultana ma wajen sau uku ta zo ta dubashi itama sun fara Jarabawar Neco shiyasa Abba yace ta zauna a gida ta natsu kan jarabawarta. Da Farko nan aka so a barta wajen Salima tunda mijinta ne ranar da Sadiq ya farfado yaji labari yace ta koma gida shi baya bukatar ta. Shikenan ta shiga damuwa tana ganin kamar ko tun abunda ya faru ne bai manta ba, shi kuma gani ya yi ina ita ina Jinyarsa ta na mace sannan shi bayason rashin kunya tunda kuma ya lura shi ta koya yanzu. Har abokansu Jb da Mb sun zo sun Dubashi suka yini kafin su tafi shi dai Shuru kawai ya ke yi baya mgana yana kwance kafafunsa sagale a sama hannanunsa ma yana Sagale sai inda aka juyasa ko wanka ba'a yi masa sai dai ana goge masa jiki bayan kowani kwanaki Biyu. Yaga kowa ammh bai ga Siya ba, tun washegarin ranar da ya Farfad'o sai da ya yi ma Big sis mganar ina Siya? Saboda lokacin da ya ke kwance yana fama da kansa ita kawai ya ke tunawa har Mafarkin ta haihu ya yi, saboda sanin Halin data ke ciki. Ita kuma Surayya ta yi ta kiran wayar Hasiya a kashe, kuma ta yi hausan karisawa zariya ta duba ta bai zo mata ba sai da Sadiq ya yi tambayar, tunanin haka ya zo mata alokacin sai aka yi baki abokan Alhaji Jibril tare da su Abba suka shigo tunda ita ta na yawan zuwa duba Sadiq din. Fitan ta yasa tace ma Auwalu bari taje ta dawo  daga nan ta hau motar Zariya sai gidan Hasiya. Sai dai Labarin da taje ta iske ya tada mata Hankali bata tab'a tunanin Umma zata iya sa su sajida su zo su aikata irin wannan aikin ba. Maman suhailat ta samu, abunda yasa ma ta gayamata cewar da tayi ita yayar mijin Hasiya ce, shine Dalilin da yasa Maman suhailat ta kai ta dakinta ta zayyana mata komai. Da Surayya ta tambayeta yanzu Hasiyar ta na ina? Maman suhailat tace washegarin tafiyata taje gidan yayata ta iske mijinta shi ya gayamata yayar mahaifiyarmu ta rasu mun tafi can garin inda mahaifiyar mu ke zaune. Kuma yace mata sai bayan an yi kwana bakwai zamu dawo, Hankalin Surayya ya gama tashi ta rasa wata amsa kuma zata baiwa Sadiq in ya kara tambayata Hasiya? Ba ta baro gidan ba sai da ta Rubuta ma maman suhailat lambarta tace da zarar taji Labarin dawowarmu ta kirata ta sanar da ita. Sai da surayya ta fito zata tafi ne Maman suhailat ta Biyo ta tana tambayata  jikin Abubakar din? Ita kuma tace mata yana ta samun sauki sai hamdala. Surayya ta koma asibiti cikin Tsananin Damuwa, Allah yasa lokacin da zata yi ma Sadiq sallama su Abba na wajen tare da shi ma za su koma Shiyasa ta samu ta sulale a lokacin har suka isa Gusau ta na mamakin abunda ta aikata ashe kenan Fad'an da akace mallam ya zo ya yi mata bata ji ba tunda tasa a yi ma Hasiya wannan Tozarcin. Kuma ta yi alkwarin ko a Fuska bazata nuna musu tasan abunda suka aikata ba zata bisu a haka ita damuwar d'aya Sadiq. Shi kawai take Tunanin hanyar da zata sama masa mafitan da bazai san me ya ke faruwa ba. Ta kara komawa ganinsa a lokacin ne da ya kara tambayarta ta yi masa karyan ai tazo ta gansa lokacin yana barci saboda nauyin jikinta yasa Abba yace tayi zamanta a gida. Kallonta kawai ya yi tunda bai cika mgana ba Sosai ammh ta san bai yarda da ita ba, saboda tsaro yasa har Auwalu ta shiryama ko Sadiq ya Tambayesa Wata siya tazo? Yace eh tazo yana barci har Tahir ta gayamawa. Tahir yace"To tazo din ne? Nima fa ya yi ta tambayana nace ban sani ba." Surayya sai ta kasa mgana, kawai dai tace su gayamasa tazo ma wajen sau biyu yana barci saboda nauyin jikinta yasa Abba yace ta yi zamanta a gida. Kamar ta sani dukkansu sai da ya tambayesu suka gayamasa yadda Surayya ta gayamusu. Tun daganan yasan akwai wani abu, ta yaya yaga kowa sai itace bai gani ba sai ace wai tazo yana barci kaji mganar da Hankali bazai Dauka ba. A jikinsa yasan akwai abunda ya kamata ya sani bai sani ba, shi damuwarsa d'aya tsohon ciki gareta babu wanda ke tare da ita balle ya taimaketa kuma ba ta da kowa sai shi, hankalinsa ya kan kwanta in ya Tuna tana da yan'uwa a Zariya yasan baza su barta ita kadai ba sai dai kulawarsa ne a matsayinsa na Uban cikin bazata samu ba. Sai ya rage mgana kwata kwata daga sannu ya jiki shikenan ko Tahir sai ya yini mganarsu bata wuce goma ba. Kuma abunda ya Fahimta shine ba mai yi masa mganar siya, sannan zuwan Innani ta gayamassa wani kalma in da tace wai bala'i da Annoba ya sauka a gidansa jinin wannan yarinya ba alheri ba ne. A lokacin bai damu da mganarta ba sai yanzu ya ke auna mgamganunta. A ransa yasan daman haka zai faru suna zargin duk abunda ya faru da shi Siya itace sila, kuma yana da tabbacin wani abu ya faru wanda ba'a so ya sani to bazai matsa ma kansa sai ya sani ba ammh in ya samu kansa shi zai mike yaje ya gannin ma idanuwansa komai sannan yaji duk abunda ya faru. Shiyasa ya yi bakam bai kara yi ma kowa mganar Siya ba hankalin Surayya sai ya kwanta a tunaninta in ya samu lafiya sai ta gayamasa ita kuma Umma ta samu natsuwa Tunaninta ya ma manta da ita tunda bata ya yi mganarta ba, ta manta fa matarsa ce dauke da ciki ta ya ya zai manta da ita sai kace wanda ya samu makuwa? Haka Sadiq ya cigaba da jinya a asibiti har daga ma'aikatansu daga Abuja sun zo dubashi, kuma sun ji dadin ganinsa har yana samun sauki. Yana da wata d'aya a asibitin aka duba Dorin kuma Alhandulillah duka sun yi kyau, sai aka fara bashi Sanduna guda biyu yana tafiya da su a haraban asibitin Saboda warware kasusuwansa da suka gaji da kwanciya sannan Tuni Rauninka sun fara baki sun dauko warkewa. Kansa ma an cire bandage ya sabe kumburin gabadaya. Hannunsa kuma sai dai aka sakamai jakar sagala hannu aciki, kullum yana sanye da gajerun wando saboda Kafarsa, kuma Alhamdulillah kowa yazo yaga Sadiq sai yace ba shi da kyamar jiki ganin cikin Lokaci har ya fara tafiya da taimakon sandunan asibiti. Kuma su kansu likitocin sun ce sun yi mamakin saurin mikewarsa suka yi musu albishir di'n Cewa bazai jima za su sallameshi ya koma gida ya cigaba da kula da kansa. Auwalu ke Daukan Hotonsa yana Turama yan'uwansa mata suna gani suna jin dadi, Sultana kuma koda yaushe cikin kira waya ta ke yi, in aka basa daga gaisuwa da tambayan ya jiki shikenan ya ke yi mata shuru itama sai ta rasa me zata ce ganin yadda ya yi mata gim da shi, har Umma ta gayamawa ita kuma tace ta yi masa uzuri saboda halin ciwo, ita kuma tana son shi, shiyasa har aranta taji ta tsani Hasiya umma kuma ta bata tabbacin da ita kad'ai Sadiq zai cigaba da zama a matsayin matarsa. Hatsarin nan da Sadiq ya yi sai ya rage magana kamar ba shi ba, ya koma wani shuru shuru mgana sai in ta zama dole. Fatansa kawai ya samu saukin da zai iya tafiya yaje ya duba Siya yaga Halin da ta ke ciki, in ya lissafa dai dai cikinta ya fita wata na tara ya shiga goma kuma yasan Edd dinta tun 19 ga watan jiya ne. Ga shi ba waya a hannunsa da ya yi mganar wayarsa sai aka gayamasa ta lalace ta fashe a had'arin da ya yi, tare da motarsa da bazata gyaru ba saboda yadda in jin Motar ya tashi aiki Abba yace a saidata kawai tunda bazata gyaru ba. Shi dai bashi da tacewa sai shuru, tunda ana ganin yana kwance ba shi da lafiya in ya matsa da mgana sai kuma ace shi da ba shi da lafiya. Ammh ya shirya yin abunda rai bazai so ba, matukar ya warke yaga abunda bashi ne ba. Jinya dai ta yi tsawo kad'an ba da yawa ba, tunda har kusan wata Biyu Sadiq yana asibiti sannan aka sallameshi lokacin yana da wajen kwana sittin da wani abu a gadon asibiti yana jinya. Direct daga nan sai Gusau gida aka wuce da shi, a kuma bangarensa yace a kaisa tunda Abba ya basa zabin cewa ko gidansa za'a wuce da shi yace a'a a wuce dashi gida. Kafar ne kawai ta rage hannu kuma ya warke shima sai kad'an da ba'a rasa ba kuma an cire masa wannan Jakar kafar ne ya ke tafiya da taimakon sanda har a lokacin. Dayake tun a asibitin ana yi masa aski, da ya dawo gida wanka kawai ya yi, sai kuma aske gashi nan da suka taru a jikinsa har kuma Lokacin Auwalu na tare da shi duk Sadiq din yace ya koma gida zai iya kula da kansa ammh yaki yace yana tare dashi har sai ya warke gabadaya. Umma tafi kowa Farinciki da dawowar Sadiq gida ya ji sauki gida haka ya ke cika da yan'uwansa duk kuma a bangarensa ake zama Har Innani ta koma yini a bangarensa. Shi dai baya mgana Sosai sai dai ya bisu da ido kawai kuma sai ma da ya dawo gida ya kara tabbatar da zarginsa. Siya suka dorama alhakin duk abunda ya sameshi. Abba ne ma daya dawo hayyacinsa a kwanakin baya ya yi ma Surayya mganar Hasiya ita kuma ba kwana kwana ta sanar da shi abunda Umma ta aikata da taimakon ya'yanta. Abba ya shiga tashin hankali yace maza maza ta sake komawa Zariya ta tabbatar ta samu Hasiya domin taga Halin da ta ke ciki. Ita kuma a ranar data shirya zata koma Zariya uwar mijinta ta rasu ba Halin tafiya kuma sai abun ya shafe a ranta gabadaya. Shi Uban gayyar bai manta ba sai da ya yi kwana hud'u da dawowa gida sannan Tahir ya zo dubashi, kuma akaci sa'a Tahir yazo da mota kirar Camry, Motar uban gidansa ba ya kasar shine ya ke zirga zirgan shi da ita. Yana zuwa Sadiq yace zai kai sa wani waje a motar don Allah, shi a tunanin Tahir nan kusa ne shiyasa bai ce a'a ba, Sadiq ya shirya cikin riga da wando na wani farin yadi, sai ya nannad'e kasan wando, saboda Kafarsa ta dama kuma Tahir yaga harda Hula ya saka baki sake yace"Wai ina zaka je ne? Kai Tsaye Sadiq yace"Kai dai muje zaka ganin ma idanuwan ka" Ba musu Tahir ya tashi suka tafi, kuma abunda Sadiq ya shirya ba wanda yasan ya fita ya riga ya gayama Auwalu duk wanda yazo dubashi yace yana ciki ya kwanta Malam Taju megadi Sadiq ya fad'a masa ko Abba kada yasan ya fita. Sai da suka dauki hanya ne Tahir yace ina zamu je? Sadiq yace"Zariya." Tahir ya saki baki kafin yace"Ka yi me a Zariyan? Kai Tsaye Sadiq yace"In yi me kuma? Ai kasan dai ina da wata matar acan." Tahir sai ya kasa mgana duk da Big sis bata gayamasa komai ba ammh yasan akwai matsala kuma dai maganar gaskiya shi bai ganta ba, a ransa yace to Allah yasa ba rasuwa ta yi wajen haihuwa ba sai yaji a ransa yana fata da addu'an komai lafiya saboda yasan yadda Sadiq ke girmama waannan zabiyar matar tashi. Sai ga su a Zariya har kofar gidan da Hasiya ke zaune cikin kuma sa'a suka ga Maman suhailat a waje an kawo mata sakon kaya daga kano. Tana ganin Sadiq ta iso wajensu bakinta har kunne ta na Fad'in"Barka da arziki Abubakar Allah sarki daman nace in dai kana raye zaka tako kafarka wajen Hasiya." Mirmishi kawai ya yi mata sai barka da arziki ta ke yi masa ganinsa da Sanda har tana kwallah. Tun kafin ma ya yi mganar Hasiya maman suhailt na sharan kwallah ta kwashe duk abunda ya faru ta gayamasaa. Cikin tashin hankali yace"Yanzu ina Siya ta ke? Maman suhailat tace"Ta na gidan yayarta din nan fati, ba ta ma jima da dawowa ba da farko ta na wajen mahaifiyar tasu ne kasan yayar mahaifiyar ta su ce ta rasu kwanakin baya." Har tana gayamai itama daga baya ta koma sai ta samu Hasiyar ta dawo nan cikin Tausayi tace"Abunda zai baka sha'awa da yarinyar nan duk abunda ya faru bata gayama yan'uwanta komai ba, cewa ta yi kayi tafiya baka gari ita kad'ai ce ta kunshi wannan bakincikin baiwar Allah. Ai Sadiq bai gama sauraranta ba ya fad'a mota saboda bacin rai baya ma gani sosai. Huci kawai ya ke yi, Tahir ma ya shiga ya tada motar Sadiq na nuna masa hanyar gidan, Tahir ganin yadda Sadiq ke huci yasa ya kallesa yana fad'in"Ka bi a sannu Sadiq ka san dai baka da lafiya ko? Sadiq kamar ya yi kuka yace"Tahir wannan wani irin tozarci ne? Ni ne basa son ganin farincikina ai shikenan dama a hatsarin da na yi mutuwa na yi da kowa sai ya duka ya Dauka." Da Sauri Tahir yace"Subhanallah kada Bacin rai yasa ka yi Sabo mana." Sadiq bacin ransa da Maman Suhailat tace har Surayya ta zo kuma ta gayamata ammh shine ta yi masa karya. Ba dad'ewa sai ga su a kofar gidan Adda Fati Tahir ne ya buga sallama shi kuma Sadiq na gefe rike da sanduna zuciyarsa na faman Bugawa. Mijin Adda Fati ne ya fito ganin Mijin Hasiya yasa ya fito da sauri sun gaisa sama sama shi da tambayan garin yaya ya samu rauni a bakinsa shima Sadiq a bakinsa da tambayar ina Hasiya? Mijin Adda Fati ya yi ajiyar rai kafin yace"Suna asibiti da Hasiyar tun safe ta fara zubar da jini, ammh yanzu Yayarta ta kirani tace C.s Za su yi mata yanzu nan." Sadiq ya ji kamar ya zura a guje saboda Tashin hankali cikin Sauri da rawan baki yace"Wani asibiti ne? Yace"Kamar inda ta ke awo tace na manta  sunan asibitin." Sadiq ya juya da sauri yana ce ma tahir yasan asibitin su tafi kawai. Sai mijin Adda Fati yace shima daman can zai je, kawai sai suka rankaya gabadaya. Suna tafe Habibu mijin Adda na basu Labarin irin wahalar da Hasiya ta sha, tafi sati daya ta na nakudar tsaye sai yau da safe ne ta fara zubar da jini yasa suka tafi asibiti da Sauri ashe ma haihuwar ta ki Sai an yi mata aiki. Asibitin musulmi ne, suna zuwa Habibu ya kira Adda Fati sai gashi ta fito Yarkace yarkace fuska duk ta kod'e Saboda kuka da Damuwa. Itama sai da ta bude baki ganin Sadiq cikin damuwa tace"Abubakar ashe ka dawo? Subhanallah ba dai a wajen aikin ne ka samu raunika haka ba? Sai ya ma kasa yi mata mgana yana jin wani abu na shiga ransa. Ya kalli Tahir shima ya kallesa karshe dai Tahir aka bari da fadin"Eh a can ne ya samu d'an hatsari kad'an". Ta bishi da Allah ya kara lafiya suna tafe ta na fad'amai daman saka hannun mijinta ake jira ko na wani makusancinta zasu shiga da ita tiyata sun ce yan Biyu ne acikinta. Akwai bukatar gaggawa ceto Rayuwarta da na abunda ke Cikinta. Shiyasa bata lokaci suna zuwa Adda Fati tace ga mijinta nan Sadiq ya Rattafa hannu aka shiga da Hasiya Tiyata, Sannan kudin Tiyatar ma shi ya Biya bai zo da ko Atm dinsa ba tunda shi babu komai ma a hannunsa Tahir ya ara masa kudin hannunsa ya Biya da shi. Tare suka yi zaman jugum jugum a asibitin nan shi da Tahir da Adda Fati tare da Adda Rukayya, sai Habiba da Ramatu mijin Adda Fati Shi kuma ya tafi daga baya, sannan Safiya tazo daga baya sai kuma yar'uwata Sister Zainab da ke aiki a asibitin. Sadiq ya yi kwallar Tausayin Hasiya ciki har wajen wata sha daya yana jikinta bata haifeshi ba  sai yanzu ga nauyin jiki  ga na zuciya ga na lulura ga tashin hankali ammh ko alama bata zaunar da wani cikin yan'uwanta ta b'ata shi ko danginsa a wajensu ba, sai yaji matsayin da Siya ke da shi a baya yanzu ta na Hau hau sama da matsayinta na baya acikin zuciyarsa. Kimanin awa uku sannan aka Samu nasaran fito da Ya'ya biyu duka maza acikin Hasiya yan biyu kosassu masu lafiya wad'anda ke kama sak da mahaifinsu sai dai Farar Fatar Hasiya kad'ai suka dauko. Ita kuma ba ta farfado ba an kaita dakin Hutu. Sadiq na gefe yana yi ma Allah kirari da godiya. Tahir ya amshi yaron bayan su Adda sun gama ganinsu suna hamdala. Adda Fati ta yi gefe ta kira Amma tana gayamata an yi ma Hasiya aiki an ciro mata yara maza guda biyu. Amma sai farinciki da hamdala kuma daman ba su gayamata Hasiyar na naguda ba, kada su tada mata hankali. Kamar Amma na wajen tace"Allah Sarki Ina shi megidan nata ya dawo kuwa? Adda Fati tace"Ya zo a kan gaba Amma, shima ashe achan in da suke aiki hatsari ya samu." Amma ta yi ta salati nan tace a bashi wayar shi kuma Lokacun yana gefen Tahir da ke nuna masa yaran shima bakinsa har kunne. Adda ta mika masa waya tace ga Amma cikin ladabi ya karb'a ya gaisheta lokaci d'aya yana yi mata gaisuwan Adda Tunda Maman suhailat tace yayar mahaifiyarsu yasan Adda ce tunda shi dai ita kad'ai ya sani." Amma ta amsa masa, itama ta yi masa jaje tare da barka da arziki sannan suka yi sallama ya mikama Adda Fati wayar. Shi bai yi ta yaran ba sai da ya tambayi likita yanayin jikin matarsa ya tabbatar masa zuwa dare Hasiya zata Farfad'o cikin koshin lafiya. Sannan ya karbi yaran hannun Tahir sun ci Kayan sanyi na yara masu kyau, Allah yasa Hasiya ta kwashi wasu daga cikin kayan haihuwanta ranar da su Sajida suka koreta suka karbe key din dakin. Kuma daman wasu kayan akwai biyu biyu wasu kuma daman Both sawar maza daa mata ne. Tahir na gefe na daukansu Hoto cikin murna yace"Abokina ga jinjina." Ya fad'a yana sara ma Sadiq shi kuma yana mirmishi tunda bashi da kafa, sai da ya zauna Tahir ya Dora masa yaran a jikinsa. Kallonsu kawai ya ke yi yana jin wani Farinciki daman haka ake jin in mutun ya zama Uba. Addu'a ya ke ta tofa musu sannan Tahir ya kama masa dayan ya rike dayan ya yi musu kiran salla duka kunnuwansu kuma ya sanya musu suna batare da ya Furta ma kowa ba. Aka bar Tahir da fadin"Ashe ashe shiyasa ka dage, ashe akwai rabon yan Biyu zarata kai da yar Zabiyar ka." Hararansa Sadiq ya yi kafin yace" Sunanta Asiya mallam ba zabiya ba." Tahir ya kwashe da Dariya yana fadin"To yau kuma sai ta koma Asiya ba Hasiya ba." Yana jinsa ya yi masa banza, yaran nan sai da Nurses suka zo suka Daukesu suka maida su ciki sannan suka bar hannun Sadiq. Adda Fati kuma taje gida ta kawo ma Hasiya wasu kaya tare da Ruwan zafi. Su kuma su Sadiq suka tafi salla domin ba su yi azahar da la'asar ba har Biyar na yammah ya wuce Sun idar da sallar kenan Abba ya kira wayar Tahir. Tahir na gani yace"To an fa gane baka gida." Sadiq ya karb'i wayar yana fad'in"Ba ni zan dauka." Ba musu ya mika masa shi ya amsa kiran. Abba daman suna shashen Sadiq ne an turke Auwalu dole ya fadi gaskiya Umma ta kasa zaune tsaye itace daman ta fahimci Sadiq baya gidan tunda har ciki ta shiga bata gansa ba. Daga karshe da Tambayoyi suka tashi kan Auwalu yace sun fita a mota tare da Tahir shine Abba ya kira Tahir shi daman su suka kirasa suka tadamai Hankali kada Innani da Umma su ji Labari. Abba na jin an dauka yace"Attahiru kuna ina ne kai da Abubukar? Sadiq yace"Ba shi ba ne, ni ne Abba." Abba yace"Magajin gida lafiya? Ina kuka je? Sadiq yace"Zariya Abba." Abba ya maimaita"Zariya? Da yasa gabadaya su Umma suka mike suna kallonsa gaban Umma na fad'i. Dagacan bangaren Sadiq yace"Eh nazo na iske Hasiya na asibiti zata haihu, sai dai Mungode ma Allah tunda an yi mata C.s an ciro mata mazaje guda Biyu." Abba ya washe baki cikin Fara'a yana fadin"Alhamdulillah masha Allah, ina ita uwar fata ta na lafiya? Sadiq yace"Eh bata dai Farfado ba dai har yanzu muna asibitin tare da yan'uwanta." Abba ya Shiga addu'ar Allah ya bata lafiya ya yara abunda aka samu. Sannan suka yi sallama. Abba na sauke wayar a kunnensa mama ta ce"wa ye kuma ya haihu Abban siyama? Cikin Tsananin Farinciki yace"Matar Magajin gida ce ta sauka, aiki aka yi mata an ciro abokaina har guda Biyu." Umma sai ta zaro ido, Mama kuma sai tace"Allah sarki.! Innani kam sai kabbara cikin Dariya tace"Ni"imar Ubangiji da rahmarsa ya sauka a gidan magajin gida Allahu akbar" Sai kuma ta kasa kuka tana fadin ashe tana raye zata gani. ita innani abunta kamar na yan juju ne nan Umma ta gayamata ta saka an koreta tace gwara da akayi haka ammh yanzu ance an sauka tace Rahma ta sauka a gidan magajin gida. Umma mamaki ya hanata kara mgana kenan yarinyar nan sai da ta kara kusantar rayuwar Sadiq ita tana Tunanin ta rabasu ashe hakan ta bai cimma ruwa ba..kafin kace kwabo kowa yaji Sadiq ya samu karuwar yan Biyu. Sultana da siyama da suka Dawo daga Jarabawa suka samu Labari. sai kishi da bakinciki ya turkuketa har da kuka Siyama kuma sai ta kama Murna tana son ganin yaran kuma ma yan Biyu masu ban sha'awa. Surayya da ta samu Labari ta fi kowa murna daman kuma tasan girman cikin nan na Hasiya yafi guda d'aya. Bata yi mamakin jin cewa Sadiq yana zariya ba, daman tasan matukar yana iya tafiya sai ya nemo Hasiya zuwa kuma wannan lokacin tasan yasan komai da ya faru. Da wayar Tahir ta kirashi suka yi mgana da shi ta yi masa barka, bai yi mata wata mgana ba itama bata yi masa ba sun Rabu akan gobe zata zo in sha Allahu..shi kuma yace zasu kwana a Hotel zuwa da Safe tunda Hasiyar ta Farfado dazu bayan mangariba. Ni dai kawai farkawa na yi na ganin a gadon asibiti acikin daki na musamman. Nurse din da ke kaina ta shaidamin aiki aka yi min an ciromin yara Biyu duka maza. Ba farincikina Haihuwanta na rika yi ba sai na ganin Assadiq a kaina yana rike da Hannuna. Sai gashi ina hawaye ina fadin"Assadiq daman zan kara ganin ka? Cikin mirmishi yace"Gashi kin gani, ai na taba fad'a miki ni da ke har Abada ne Siya." Duk da dinkin jikina sai da na Rumgumesa ina kukan Farincikin sake ganinsa a Lokacin da na Fidda rai. Ban taba ganin Tahir ya yi min Fara'a irin na yau ba, shi ya mikama min yaron d'aya Assadiq ya kwantar da daya a saman jikina. Su Adda na gefe suna ta min mirmishi da barka da arziki. Bansan Sadiq na tafiya da Sanda ba sai da ya mike cikin damuwa na kallesa ina fadin"Assadiq me ya samu kafar ? ita bata warke ba?. Domin duk naga Tabon ciwukan kansa cikin mirmishi yace"Karayace a kafar ita bata karisa warkewa ba." Sai gani hawayena na diga saman ya'yan dake zube a jikina. Mirmishi ya yi min kafin ya Furta"Nagode Nagode sosai Siya, na yaba kuma ina Fatan Ubangiji kema ya yaba miki fiye da yadda ni na yaba miki." Na kalli yan'uwana a zagaye dani abun Farincikina ganin Assadiq a kusa dani, na tuna a baya sanda na shiga cikin kunci saboda rashinsa. Har nagama zamana a wajen Amma bata san abunda ya faru ba, saboda kada ta Fahimci wani abu yasa nace zan dawo wajen Adda kafin Assadiq ya Dawo. Itama da na dawo ban gayamata komai ba, har kuma zuwan Maman suhailat ni nace kada ta sanar da su, hatta kawata Ramatu na Boye mata wannan sirrin Saboda ba na so su rika kallon Assadiq da wani Duba na Dabam. Safiya kawar Amana ce bata tafi gida ba sai da taga farfad'owata na Tuna gajiya ta yi da kiran wayata a kashe taje gidana maman suhailat tace ina gidan yayata daman kuma mun taba zuwa tare sai gata tazo ganina, da ya ke mun koma makaranta a halin nauyin cikin nan da na ke ciki tara kani makaranta naje na karbo T.P LETTER d'ina ban dai samu na kai makarantar da zan yi Teaching pratice din ba Nagudan Tsaye Tsaye ya kamani, daman kowa na mamakin girman cikina sannan kuma ya wuce wattanin haihuwansa. Kuma da na dawo naje asibiti suka Dubani sukace lolacin haihuwata bai yi ba, duk da cikin ya wuce wattaninsa ba su ga alamun mahaifa zata Bude ba. Yadda gabadayansu suka zagaye gadon da ni ke kwance ne ya sakani kwalla, naji a raina ni Ubangiji ya gama mini komai tunda ya barni da Soyayyar yan'uwana tare da gwarzon miji irin Assadiq Daman na sani ko  a jima ko a dad'e Assadiq zai zo ya neme ni shiyasa nima na kasa mantawa da shi acikin zuciyata. *Janafty* *TMWB3K012* *TMW is a paid Novel, Pay 500 for regular or VIP N1K, Via 0552179550 Jamila Umar Gt bank, 09069067488* https://chat.whatsapp.com/K3rO5UonX4GDVxtQbA5mZl PAID ADVERT✅ Assalamualaikum wa rahmatullahi ta'ala wa barakatuhu!!! Wannan group din dai na komai da komai ne. A taiqaice *Farashin mu na daban ne compared to sauran Yan kasuwa *Kaya masu kyau da quality. Abinda kika zaba shi za a Baki * Swift delivery.watau waybill a sauqaqe da Yardar Allah * Muna sake New Arrivals ka fin su cika Gari * Muna iya duba maku kaya a good price ko da ba namu ba ne idan kuka Aiko da hoton kayan Allah sa mu qaru da juna Ameen Washegari Surayya da ta shirya tafiya Zariya sai da ta biya ta gida ta sanar da Abba zata je ta duba mejego da yara. Jin haka yasa Abba yace Mama ta shirya sai su tafi tare da Surayya sannan yace nawa suke bukata wanda zasu iya rike ma maijegon wani abu? Ita daman Surayya ta zo da kaya cike da leda su pamper din yara ne, sai Kayan sanyi masu kyau da mayukan setin na yara. Sai sauran tarkace irin na kayan yara dai jariri, Jin Abunda Abba yace ne yasa tace ya bari wannan sai sun je sun dawo tukunnah. Siyama ma jin da Mama Za'a tafi ganin Twins itama ta dauki damara tace sai taje daman da Tunanin yaran ta kwana a ranta, Innani kuma damam Tun jiya ta had'a kayanta tace ai magajin gida ya yi mata alkwarin ita zata yi ma Hasiya wankan jego saboda haka rana fa bata karya sai dai uwar diya taji kunya. Shi kuma Abba yace a tafi da ita taga ya'yan magajin gida Umma kuma sai ta zama yar kallo Sajida ma tazo gidan gulma taga ko Surayya ba ta tsaya cewa tazo su tafi ba, ballatana Abba da ga ita har Umma sai ya yi kamar bai ma gansu ba, harda Sultana da ta damu kanta da bakin kishi Saboda Haihuwar Hasiyan. Direban Abba ya tukasu zuwa Zariya ko da suka isa ba su iske Sadiq ba ance ba jimawa suka dauki hanya shi da Tahir, sai wayar tahir din ta kira ya bashi suka yi mgana. Ita kanta tasan Sadiq ya riketa a ransa saboda ko alama a muryansa ba wannan Fara'a da sakin jiki in yana magana da ita kuma a jiyan ta fad'a masa yau zata zo ta duba mai jego ammh yaki Tsayawa su iso. Sunan asibitin ma Tahir ta kira da Farko ya fad'a musu da sunan lambar Dakin kafin su isa sannan suke samun Labarin Sadiq din ya Dauki Hanyar komawa Gusau. Shi ko daman ya riga ya yi ma kansa wani alkwari acikin ransa, in dai abunda ya shafi Siya ne ya Cire kowa a ciki shine mijinta kuma Shine Dolenta ba wasu yan'uwansa ba, Abba ne kawai da Umma suka zame mata Dole suma sabama Ubangiji ya danne Bin umarninsu. Shi daman Tunda ya samu had'arin nan da kuma jinyar da ya kwanta ba komai daya danganci katunan bankinsa a hannunsa, shiyasa ba shi da kudi sai ya yi ta aron na Hannun Tahir wanda shima yace ba na shi ba ne na ajiya ne, Kamar Abba ya sani da Safe ya kirashi suka yi magana yace ya Turamai account din bankin tahir ya Tura masa 100k. Da shi ya samu ya yi ma Siya siyayyan kayan titi, kayan yara na pampers da Sauran su, tunda komai na haihuwan da suka tanada na cikin Dakin nan kuma sun tafi da key d'in. Sai kawai ya bama Adda Wasu kudi yace taje kasuwa ta siyo abunda babu kafin yasan abunda zai yi akan su Sajida. Ko zuwan su Surayya Abba ya fad'a masa ammh ya ki tsayawa Saboda bai ga abunda Tsayawar nasa zata haifar ba shiyasa yace su koma kawai. ya so ma Tahir ya barshi ya hau motar haya shi kuma sai ya wuce Daura ammh yace a'a bai gama warkewa ba yana Tafiya da sanda bazai barshi ya yi Tafiya mai Tsawo a motar haya ba. ****** Nayi matukar Farinciki ganin Anty Surayya, acikin raina nasan ya'yana a kallah suna da masu son su daga dangin mahaifinsu. Innani kamar ta lashe yaran nan ta yi kuka kafin su tafi bata san iyaka ba sai ta kallesu sai ta koma ta na jan majina tana fad'in"Allahu akbar Ashe ina da Rabon ganin tsatson magajin gida ban mutu? Mangaganu dai an sha su kamar ba Gobe sun yi ta tsiya da Siyama wacce tace Innani ta hanata ganin ya'ya. Innani ta balla mata Harara kafin tace"Kaji min rashin kunya, to an hanaki ganin su d'in, in kin ji Haushi sai ki yi aure ki haifi naki." Siyama sai hawaye Adda Fati ce ke faman bata Hakuri innani ko sai ta fara masifa Surayya na gefe bata ce komai ba ballatana Mama da in ta Tofa tasan nata sai yafi zafi. Ba su wani dade sosai ba sallar azahar kad'ai suka yi da Adda Fati ta yi tayi suje gidanta su huta su ci abinci Anty Surayya tace za su tafi ne kada su yi dare. Ita dai Surayya ta yi karan cewa Umma na yi min barka na amsa ba wai domin na yarda ba, Abba dai da tace na aminta tunda kafin Tafiyar Assadiq ya had'ani da shi a waya ya yi min sannu ta wayar Tahir. Siyama ce ta bani mamaki itama da ko maganar arziki bata tab'a had'amu ba sai ranar. Kuma ta yi ta daukan yan biyu Hoto a waya sai da tagaji, Surayya ta kawomin kayan da ta taho da shi Inna talatu ne ke ta yi musu godiya Tunda ko a jiyan ita ta kwana dani a madadin Amma. Wajajen Biyu da wani suka juya sai dai an sha daga da Innani Domin tace ita bazata tafi ba jego tazo yi min. Dakyar ta yarda suka koma da ita dacewa ta bari in taje ta gama Had'o kayanta gabadaya sai ta dawo. Anty Surayya ta bani kudi 10k tace na rike a Hannuna kafin ta Dawo yadda bata min maganar abunda ya faru ba nima ban yi mata ba duk da dai nasan tasan abunda ya faru d'in. Sai bayan tafiyarsu ne su Adda Fati ke hirar Rigimar Innani, ina dariya nace musu haka fa take, Assadiq na bani Labarinta Akwai aikin Tsufa a tare da ita. Sai kuma suka koma mganar Mama da Anty surayya ce, sukace ta na da kirki duk da ba su san abunda ya faru ba ammh sun san cewa Dangin Assadiq ba su karb'eni ba. Ni dai nayi shuru ban yi mgana mganar ma tawa ta karfin Hali ce tunda ruwa kawai na fara sha, likita yace sai da safe zan fara cin wani abu mai nauyi haka. Bani da waya a hannuna shiyasa ban yi waya da Assadiq ba, ammh mun yi mgana da Anty Surayya tunda ta karb'i lambar Adda Fati ita ta kira da Daddare muka yi mgana na yi musu bangajiya. Assadiq kuma sai washegari can da rana ya kirani da layinsa, ashe ya siya wata wayar ce sai ya saka layinsa, tunda wayarsa tasa da Atms dinsa da I.D card dinsa da aka gani wajen da Had'arin ya faru ya na Hannun Abba sanda ya koma ajiyan a daran tun kafin ya yi mgana Abba ya Dauko masa ya bashi shine da Safe ya siya sabuwar waya ya saka layinsa a ciki. Haka na cigaba da zama a asibiti karkashin kulawar likotici, tare da yan'uwana Amma dai bata zo ba tace ga Inna talatu nan tare dani. Sai dai matar Hamma Isuhu da Sauran matan kannensa sun zo sun dubani sun yi min barka suka koma. Sannan matan Baba Tanko ma sunzo tare da wasu daga cikin ya'yansa. Na yi mamakin inda suka samu Labari sai gashi suna fadin a bakin Baba Tanko su ka ji, shima yace Alhaji Jibril ya gayamasa na haihu kuma yan biyu ni kuma nasan a cikin gidansa yaji Tunda surukarsa kanwar Assadiq ce. Su ba su yi wata mgana ba sai da Adda Fati ta kira Goggon kona ta fad'a mata ranar da na ke da kwana Biyar a asibiti sai gata tazo da yammah,. A bakinta na ke jin yan'uwana Suka san yan'uwan Assadiq ni suka d'orama Alhakin Hatsarin da ya same shi. Na yi ta jin Tsoro kada ta fad'i wata mgamar da zai saka su Fahimci abunda ya faru sai kuma bata fad'a ba. Illah Adda Rukayya da ta yi Tsaki kafin tace"wannan ba bakon abu ne goggo. Abu ya sha faruwa a d'orama Hasiya alhakin abunda bata ji ba, kuma bata gani ba." Goggo ta tabe baki kafin tace"To mutane fa suna amfani da abunda suke gani yana faruwa ne." In da Allah ya taimakeni ba ta dad'e ba ta tafi da mgana ta fasu, kuma sai har bayan tafiyarta ba wacce a cikin su ta d'aga maganar tunda daman na fad'amusu abunda ya faru zuwana Gusau a karo na Biyu. Sai washegari ne da Adda Fati tazo kamar daga sama ta jefamin Tambayar a ina Sadiq din ya samu hatsarin da ake kokarin d'oramin laifi? Kai tsaye nace achan inda yaje aiki ne, bansan karyan da zan yi a gaba ba shiyasa na yi shuru da bakina, Sannan game da key din dakina karya na yi musu nace ya bace bansan inda ya ke ba, kuma na tabbatar musu ko Assadiq ba shi da wani key a hannunsa. Duk da akwai kayana da yawa acan sai Adda Fati ba ta maida kai ba, ganin har alokacin ina asibiti sannan ga Assadiq ya bar mata kudi kuma na kara mata kudin da Anty Surayya ta bani a Hannuna. Kuma koda yaushe tana kirana tana jin Lafiyata ni da Twins ita da Assadiq. Safiya ma kusan kullum sai tazo ganina sai a lokacin naga Khairiyya yayarta tare da Mamansu zuka zo dubani tare da ganin yan Biyu. Ana gobe za'a sallameni Assadiq ya zo shi da Abba da kuma Baba Sammani sai Mallam Shitu da Auwalu da Ranar da Assadiq ya koma Gusau shima ya koma gida. Ba ni kad'ai naji dadin Zuwan su ba harda su Adda Fati, duk da ba su dad'e  ba domin iyakarsu awa daya suka juya Assadiq ya sake siyamin kayan Tea da madaran yara da likita yace Saboda ruwan Nonon ya yi musu kad'an dole za'a rika had'a musu da Madara. Bamu yi wata mgana ba illah Tambayarsa da Adda Fati ta yi in da zasu kaini bayan an sallameni yace a kaini gidanta bayan suna in an samu wacce zata zauna dani sai na koma Dakina na cigaba da Jego na. Kudi haka su Abba suka bani masu yawa ni da yan Biyu ballatana da Assadiq yace tun ranar da aka haifesu ya saka musu suna Sulaiman da Muhammad. Wato sunan Babana da sunan Abba, sai ga bakin mu ya ki Rufuwa ni da Adda, Abba ma ya yi ta saka albarka har a fuskarsa ya nuna jin dadinsa su mallam shitu ma suna ta saka albarka tare da fatan lafiya mai Dorewa dani da yaran gabadaya. Washegari likita ya sallameni bayan ya bani dokoki saboda mikin dake jikina, kenan kwana shida na yi a asibitin gidan Adda Fati kuma aka wuce dani Direct dakin da Habiba ke kwana aka saukeni ni da yarana a ramar kuma Inna talatu ta saka Ruwan masu zafi ta yi ma yaran nan wanka suka yi ta tsala ihu nima kuma ta iza keyata zuwa bayi ta gasamin jiki na sosai ina wash wash ta na fadin kwana nawa na yi a asibiti da d'anyen jiki ba gashi ballatana wanka sai dai gogemin jiki kawai suke yi acan. Bani da zannuwa Atamfa Adda Fati ta siyamin guda d'aya ta farkamin zannuwa uku ina sakawa, su kuma jarirai Adda Fati ta shiga kasuwa ta kara siyo musu wasu, kuma daman dayan akwatina duka kayan haihuwan da Anty Surayya ta siya ne aciki, Anty surayya washegarin ranar da aka sallamomi ta dawo ita da Anty Sa'ima ta zo min da Ferfesun kayan ciki mai yawa tare da Kayan jarirai sannan kuma ta ce ta zab'o ma ya'yanta sunayen yan gayu, Asif da Asim tace zamu rika kiransu Saboda Sakayawa. Da ita ma mun yi mganar taron suna tace Sadiq yace sai sati ya zagayo za'a yi taron suna, bayan kuma ita cikin yan'uwan Assadiq ba wacce ta kirani sai Anty Saddiqa daga kebbi sai kuma Saliha da ita ba sau daya ta kirani ba sai Anty Sa'ima ta kirani Lokacin muna asibiti ina jin Anty Surayya ke ba su Lambar Adda ta nan suke mgana da ni. Sun tafi da cewar sai ranar taron suna za su dawo in sha Allahu. Sun tafi kenan ba jimawa sai ga Salima ta zo ita da Zahra'u da Fathihatu sai ya'yan gidan Baba Tanko su suka rakaso gidan Adda Fatin tunda ba su san gidan ba..ni na ke gayama salima zuwan su Anty Surayya nace mata yanzu suka tafi sai ta kirasu a waya sukace ai sun kama hanya sai ranar suna za su dawo. Salima sai ta koma gefe da Zahra'u ne da Fathihatu muka yi ta hira suna ta santin yara sai dai abunda na Lura itama Salimar kamar cikin gareta. Kuma da alamu tana son yara domin haka ta Daukesu ta na ta kallonsu ta na mirmishi. Kuma ta yi ta daukansu Hoto, Da ta tambaayi sunayensu Habiba ta gayamata, sai tace ga sunan da Anty Surayya tace a rika kiransu ta yi mirmishi tace sunan ya yi. Sun jima tunda Sai bayan la'asar suka tafi sukace mim sai ranar suna bayan sun gayamin sakon Hajiya Murjanatu tace tana yi min barka kafin tazo. Zuwa Lokacin nasan haihuwata ta zaga gabadaya dangi, kuma da karin yan Biyun da na haifa yasa gidan Adda Baya Rabo da Jama'a. Maman suhailat ma bata sani ba bata nan ashe tun washegarin Ranar da su Assadiq suka je ta yi tafiya, sai da ta dawo sannan tazo Dubani ni da twins ta na bani Labarin zuwan su Assadiq. Ni kuma nace mata ai a ranar aka yi min aiki tunda a asibiti ma suka same mu ka yi ta yi jimami. Mutanen gidanmu na samaru su mamanboy, sun ta zuwa asibiti Dubani kuma da muka dawo gida ma sun zo sau Biyu, Ramatu kuwa kusan nan ta ke yini sai da yamma ta ke komawa gida Nura baya nan na Haihu ammh ya yi min barka ta waya. ******* Ana gobe sunan Twins  muka yi waya da Assadiq yace yaso ya shigo ammh bazai samu zuwa ba sai bayan suna. Muna cikin magana sai yace zai kirani in ya gama mgana da Abba. Ni kuma daman yace kada mu yi shirin komai kudi zai Turomin na shagalin suna da komai da komai. Abunda ban sani ba Surayya ta same shi sun yi mgana da tagaji da sha mata kamshin da ya ke yi. Ammh sai da ya nuna mata bacin ran meyasa bata gayamai ga abunda ke Faruwa tun farko ba? Anty Suraya ta bada uzurin Saboda Halin da ya ke ciki yasa ta boye mganar ammh ba da wata manufa ba ne. Da haka ya sauko suka yi mgana ya ce ta kara siyamin wasu kayan fitar suna ni da Twins a dinka sannan mganar abunda za'a yi na shagalin suna ita ta bada shawaran a tura mana kudi sai mu yi komai da kanmu Tunda Hakkin mu ne, raguna ne tace ba laifin in ya siya sai su tafi dashi a ranar suna da Safe in kuma yana ganin akwai walaha ko mijin Adda Fati zai iya wakiltawa ya Tura masa kudin a siya Ragunan ya yanka da Safiyar ranar suna. Sadiq yace zai yi mgana da Abba, Har mganar Umma sai da suka yi yace Umma ko barka bata yi masa ba, shi kuma bai yi mata mgana ko a fuska bai nuna mata wani abu ba ya samu dai ta sauko ta na amsa gaisuwarsa. Har mallam zakari sai da ya kirasa ya yi masa barka. Surayya tace ya kyale Umma zata sauko a hankali ammh mganar su Sadiya fa? Ya kamata ya karbo wayar Hasiya da key din dakinta dake wajensu." Shuru ya yi kafin yace"Kyale su dani, so na ke yi naga iya gudun ruwan su." Da haka suka rabu a ranar kuma da ya yi mganar da Abba shima ya Goyi bayan haka Shiyasa da rana ya kirani yace na Tura masa lambar mijin Adda Fati da shi suka yi mgana. Raguna uku yace a siya sannan ya Turo mana isheshen kudin Hidiman suna yace muyi amfani da shi. Adda Fati da ta gayamin uban kudin da ya Turo sai da na yi hawaye na kirashi ina yi masa godiya. Sai kawai yace komai zai yi min bai biyamin kwatakwancin karamcin da na yi masa a rayuwa ba. A ranar da yammah sai ga Goggo Husai tare da babbar yar Goggo Hassu ita baza ta samu zuwa ba sai Matar Baba Sammani uwargida sun taho daga Shinkafi Domin hallatar taron suna. Assadiq yaji dad'i sosai shi daman bai ce kowa yaje suna ba wanda yaga dama ne yaje, Innani daman tace in taje suna ba mai kara yi mata wayau ya dawo da ita magajin gida shi da kanshi yace a barta acan sannan itama Siyan zai gayamata Innani zata Tsaya ta kwana Biyu in ba haka ba sai ta kara tada wani Fitinan kuma. Bayan bayan sun dawo daga sallar Mangariba Shi da Abba, sai Abba ya wuce bangarensa shi kuma sai ya Shiga bangaren Innani ya kara gaisawa da baki suka taba Hira sama sama daganan ya baro su zuwa Shashen Abba ya ci karo da Sultana Tunda aka yi haihuwar wannan ne gani na Biyu da ya yi mata. Ganin Farko zasu tafi makaramta ta gaisheshi ya amsa fuskarsa a had'e. Sai kuma yau abunda ya bashi mamaki bata yi masa barka ba daman kuma baya Tsammanin haka Daga gareta Shifa tunda ta nuna masa bata da kunya ya fita sha'aninta..bazai zauna yarinya karama na wasa da Tunaninsa ba. Kallo daya ya yi mata ya dauke kansa ya so ya wuceta ne sai yaji ta na gaishe shi sai ya Tsaya kad'an yana amsawa. Kuma ya tsaya ne yaga ko zatayi mgana yaga kuma ta wuce bangaren Umma ya bita da kallo. shifa yanzu an gama kuresa bazai kara matsa mata ta koma ba, ta yi ta zama tana Biye ma Umma har sai Lokacin da tagaji da ganinta a gabanta tace ta koma shidai kam ya Riga ya gama Tsara matakin da zai Dauka. Bangaren Abba ya shiga cikin sa'a kuma sai ga Umma da Abba sai Sadiya da Sajida daman dazu yaji muryoyinsu a shashen Umma da Rana shiyasa yaki shiga. Shifa Tun da yaji Labarin abunda suka aikatama Siya yaji baya son ko ganinsu bai kara yarda sun had'u ba kuma ya gama sanin duk masu kaunarsa acikin yan'uwansa da wad'anda suka kirasa suka yi masa barka da wad'anda suka ja da Hukuncin Ubangiji duk ya san su, kuma ya yi ma kowaccen su wajen zama. Umma ce kadai bai riketa a rai ba Tunda ita c din sha Kudun ce uwa ce bashi da yadda zai yi da ita ammh su yana da yadda zai yi da su, tunda ba wacce ta haifesa acikin su. Sannan ba wacce ta taba daukan Laluransa ballatana iyalansa. Ko a hidimar suna nan da kudinsa ne na banki tunda duk wattanin da ya yi yana jinya ma'aikatarsu duk wata suna saka masa albashinsa. Sannan Abba shi ya ba shi kudin Raguna duk da yace ya barshi ammh yace kada ma yace komai. Da su ya samu ya yi hidimarsa sannan ya Tura ma Tahir kudinsa da ya ara lokacin haihuwar siya. Sanda ya shigo ba su san da shigowarsa falon ba tunda yanzu in dai acikin gida ne baya tafiya da sanda ya fara lallaba tafiya hakanan. Sai in har zai yi tafiya mai nisa ne ya ke dogara sanda. Ba su san ya shigo ba ya yi tsaye a kofar bangaren Abba da farko ma kamar ya koma sai dai mganar da yaji Sajida na gayama Abba ne yasa ya Dakata. Karan Surayya suka kawo domin ba su da kunya. Domin sunga Abba ya yi musu Shuru haka ma shi ma, da ita kanta Surayya shiyasa suke Tunanin ba wanda yasan abunda suka aikata. Mgana suke akan taki saka su cikin Lissafin wad'anda za su tafi suna Zariya gobe Sajida ta kirata a waya taki Dauka kuma taje gidanta ta yi mata wulakanci shine suka zo suna gayamai ta ya ya zata ware su, ai suma yan'uwan Sadiq ne. Tsabar yadda mamakinsu ya kamashi sai da ya murmusa yana tsaye. Abba ne ya hangosa sai ya kira sunansa. Dalilin da yasa suka san yana falon kenan duka suka waiga suna kallonsa. Umma kuma na gefen Abba,  ita su Sadiya suka fara samu da mganar tace su gayama Abbansu itama Surayya ta rainata yanzu sai tazo gidan nan bata nemeta ba. Itama tana so Abban ya tambayeta hala ita ce uwar sadiq din? Domin taga ta zake da yawa akan Lamarin shi da bakar Annobar yarinyar nan. ita fa ba yan Biyu ba ko yan goma ta haifa ma Sadiq bazata kaunaci bala'i da Annoba a kusa da magajin gida ba. Kuma ganin daga Sadiq din har Abba sun yi banza da ita basa ma mata maganar sai ta fara rena kanta itama ta kwaso kananun maganganunta bata ta san zata bare da su ba. Karisowa falon ya yi yana gaida Umma, rabon shi da ita tun safe ta amsa lokaci d'aya takallesa kafin tace"Ya karfin jikin naka? Ya amsa mata da Alhamdulillah. Umma ta mele baki kafin tace"Ka dai rika Hutawa ina lura da kai cikin kwanaki nan baka san zama waje d'aya kada dai ka manta har yanzu jinya ka ke yi baka gama warkewa ba." Abba na gefe ya yi yar dariya kafin yace"ina shi ina Hutawa baban yan Biyu ne fa, abun alheri ne ya same shi fa sai ki ce ya koma ya zauna kuma salamatu" Jin Abunda Abba yace ne yasa Umma ta kasa mgana. Sajida ce ta kalli Sadiq kafin tace"Sadiq ba mgana" Kallonsu ya yi dukkansu a dage kafin yace"Sannun ku." Sadiya ce tace"Wai ya sunan yaran ne? Domin sun ji kishi kishin sunan yaran, har Umma suka fesama ammh bata ce musu komai ba. Shi kuma da gayya yace"Sulaiman da Muhammad" A tare suka had'a baki wajen fad'in"Allah ya raya." Dagaji ba har zuciyarsu ba ne. Shuru suka yi gabadayansu ransa sai ya fara baci ganin suna ta kuskus har ya mike kome ya Tuna sai ya koma ya zauna ya na kallon Abba kafin yace"Abba daman ina so mu yi mgana." Abba ya gyara zama yana kallonsa kafin"Ina sauraranka Abubakar" Sadiq ya gyara zama yana fadin"Lokacin da Hatsarin nan ya Faru dani ka samu Labarin Sadiya da Sajida sun bi matata har zariya sun ci mata Mutumci da Tsohon ciki suka koreta suka kuma kwace makulin dakin da wayarta har da Atm din bankinta? Ko ka samu Labari? Abba ya jinjina kai kafin yace"Tabbas na samu labari. Surayya ta sanar dani komai tun a lokacin." Ya fad'a ya na kallon Umma da ta Tsargu ta sunkuyar da kanta Su Sajida kuma sai suka fara Zare ido. Cikin gyada kai Sadiq yace"Yauwa daman dalilina na yin shuru ban Dauki wani mataki ba shine ina fama da jinya sannan aka zo aka yi ma Siya aiki na samu karuwa, kuma ni daman na Riga na gama Tarasu ne Abba zan yi musu iyaka da iyalina kada kace ban kyauta ba." Kai Tsaye Abba yace"Ka yi musu duk abunda ka yi ra'ayi, domin wannan karin nima sai naci mutumcinsu Tunda sun Tsallake Hurumin da ba na su ba." Jin haka yasa Sadiq ya mike Zumbur ya nuna su Sajida da yatsa kafin ya fara fad'in"Wallahi Tallahi kun ji rantsuwar d'an musulmi in dan ku ka kara shiga Hurumin matata sai na saka Shari'a ta yi min iyaka da ku gabadayan ku." A razane suka kallesa Sadiya tace"Eh Saboda mace za ka saka shari'a ta yi mana iyaka fa kace Sadiq? Kai Tsaye yace"Kwarai ma da gaake, ai ko a yanzu sa'a kuka ci wani abu mara dad'i bai samu matata ba da na rantse da wanda raina ke hannunsa sai na yi kararku, kuma kunsan Tsab za'a hukuntaku saboda kun Shiga Hurumin da na  ku ba, uwa uba kuma kun ci zarafinta a matsayinta ta yar Adam kuma yar kasa." Mamaki ya hanasu kara mgana sai kallonsa suke yi baki bud'e. Umma kuma sai Harara ta ke jifanshi dashi baisan tana yi ba. Cikin Fushi ya Cigaba da fadin"Ina ruwan ku da ita? Ko ku kuka auramin ita ? Ba wanda ya taba taimkamin da sisin kwabo wajen Rike ta, shine kuma zaku rika shiga cikin Rayuwata kuna min katsaladan? A kan wani Dallili na saka ku ne? In ku baku yarda da Allah ba ni na yarda da shi na kuma san duk abunda ya Faru dani mai kyau ko akasinsa daga Ubangijina ne Siya bata isa ta zama Silar faruwar wani abu gareni ba face abunda Ubangiji ya kaddaramin, Kashedi na gare ku shine ni ne dolen ku, dani ku ke da alaqa ba da ita ba, so ban  yi ma kowa Dole ya karfafa alaqa da Siya ko ya'yana ba, ku kyale ni da su ni ne Dolensu ita din matatace ni ya kamata na kula da Hakkokinta tare da Amanarta, ban kuma ce kowacce taje ta yi mata barka ba, ban kuma ce nima ku yi min ba, duk ku je na yafe wanda yaga dama ya yi abu mai kyau kansa ya yi mawa ba ni ba, ni dai karfafan Kashedi na shine ba Ruwan ku da matata in kuma baku ji ba ku sake Shiga harkaarta ku ga yadda Shari'a zata Shiga tsskanina da ku." Sajida sai ta saka kukan munafunci ta na fadin"Abba Umma kuma gani dai ko? Kuna ji yana fadin zai yi shari'a damu Saboda matarsa ko? Ai dai mu ci Darajan mu yayyensa ne muna gaba da shi." A fusace Sadiq yace"In kun girmeni ai baku halliceni ba? Ko kuma domin kun girmeni sai na zauna kuna min cin kashin da kuka dama? Ai girma ba Haihuwa ba ne, bazai hana naci zarafin duk wanda yace ni zai ci nawa zarafin ba, ko da akace bin na gaba na tare da Bin Allah, in babba bai kama girmansa ba karami na daidai da ya taka girman babban ya wuce abinsa." Umma ta gaji da jin mganganunsa ta mike ta daka masa tsawa kafin tace"Kaji kunya, kai yanzu Saboda Mace ka ke zagin yan'uwan ka?. Mace ma wata bakar Annoba wacce ta so kashe ka." Kafin Sadiq ya yi magana ya Rigasa da cewa"Salamatu ki koma ki zauna." Cikin mamaki Umma tace"Abban siyama." Kallonta ya yi yasa bata karisa mgana ba ta koma ta zauna. Shi kuma Abba sai ya kalli Sadiq kafin yace"Kyalesu hakanan ai ka yi musu iyaka, nima kuma na shata musu layi matukar ba alheri ne zai kai ku kusa da iyalamsa ba kada ku kara zuwa, sannan mgana ta karshe duk abunda kuka san kun amsa daga Hannunta ku taka da kafarku kuje ku maida mata sannnan ku tabbatar da kun bata Hakuri, in kuma ba haka ba wlh dukkan ku sai na yi mummunan saba muku" Suna jin abunda Abba yace suka fashe da kuka gabadaya wannan karon na gaske ne. Tunda ba su dauka har Abba zai Bud'e musu wuta haka ba, Umma kuma da suka Dogara da ita Abba ya hanata mgana. Sajida cikin kuka tace"Don Allah ka yi hakuri, mu fa Umma ce ta ce mu je mu koreta ba laifin mu ba ne." Umma ta kallesu ta na Hararansu Abba ya ya hade rai kafin yace"Ya rage naku, ni dai kun ji matsayata itama wacce ta saka kun zata karbi nata Hukuncin daidai da abunda ta aikata." Zasu fara magiya yace su tashi su bar masa falo. Shi daman Sadiq yana gama mganarsa ya fita ransa bace. Suka tashi suna sharan kwallah suka Fice, suna fita Umma ta kalli Abba tana fadin"Abban Siyama ai ba laifi ba ne domin na saka an kori wannan bakar Annobar, wacce ta so ka kashe mana d'a daya Tilo namiji da muka Haifa" Ko kallonta Abba bai yi ba taga ya Dauki waya ya na Dannawa ba ta ankara ba sai da taji suna gaisawa da Mallam zakari ta Rude. Tana rokonsa da ido da Hannu ammh Abba ya yi kamar bai ji ba. Ya kwashe duk abunda ta aikata ya sanar ma da mallam zakari. Dagacan bangaren ransa ya baci cikin Fushi ya fara magana Abba na jin haka ya saka mata a amsa kuwwa. Cikin ba da Umarni Mallam zakari yace"Sulaimanu ka fattake ta daga gidanka Tunda Salamatu ta zama zakka, ni kuma ka sanar da ita Tunda ni Uban banza nake gareta ta bid'i wani gidan Uban ba dai nau gidan ba ka hid'i mata haka Tunda Shawaran ki uwa take mara lissafi." Abba ya kalleta alamun kinjin dai ko sannan yace ai tana jinsa. Nan yace a bata waya ya yi ta bacinta Umma tana kuka tana bashi Hakuri ya kashe wayarsa. Abba kuma ya karbi wayarsa ya mike yana fadin"Bazan kore ki ba, ammh ki sani itace damarki ta karshe, nagaji da d'aga miki kafa salamatu." Daga haka ya tashi ya bata waje, Sai ga Umma da kuka har shashenta. Su Sajida da suka zauna ta dawo su kara zugata sai kuma suma suka ga ba Dama. Sultana dai suka gama zaunarwa suna kara zugata, Umma kam ciki dakinta ta shiga ta maida kofa. Me ta saka me ta saka oho, ta ga dai bata da mafita su Sajida ma bata san tafiyarsu ba. Tun safe ta je bangaren Abba bayan Mama ta koma shashenta ta Durkusa ta na bashi Hakuri shi kuma yace bakomai. Fatansa ta sakama auran magajin gida albarka sannan ta maida masa matarsa tace duka zatayi. Daga karshe yace bayan suna taje taga Jikokinta ta yi ma matar Sadiq barka taje to. Ta rokesa ya kira Mallam Zakari yace masa ta bashi hakuri, shi kuma yace sai in yaga da gaske ta ke yi hakurin da ta bashi Sannan zai kirashi ya gayamasa. Tana komawa bangaranta ta kira Sajida da Sadiya da Sa'adatu tace su shirya suje Zariya suna. Sannan ta kira Surayya tace ta zo gida tana nemanta. Daman kuma Surayyan zata Biyo Tunda Abba yace har da Mutanen shinkafi za su tafi Sakeena ta kira ta tace itama zata je. Ta d'an bata Lokaci tunda ta siya wasu kaya aka kawo mata daga kasuwa, Suba'atu da Saddiqq sun turo kudi a siya ma maijego kaya ita da Twins. Ta yi mamaki da ta zo Umma na bata Hakurin ta jira sauran yan'uwanta su tafi tare, sai ba ta ja ba tace su yi sauri saboda kada su yi dare kuma sai Gobe za su dawo. Bata gama mamaki ba sai da Sadiq ya Shigo Umma ta yi masa Barka da kuma saka albarka ya amsa bakinsa har Kunne yaci fararan kaya ya Fito sak angon karni karni. Kuma nan ta ke Umma ke tambayansa bayan suna Sulatana zata koma dakinta kafin dai ya koma wajen aiki. Shi yace duk yadda ta yanke daidai ne a wajensa. Sai dai bai yi kasa a gwiwa ba ya kalli Umma yana fadin"Ita Sultanan na son komawa da gaske? Umma tace"Eh mana, ni ce daman na hana kuma yanzu na saki Allah ya baku zaman lafiya gabadayan ku." Sai amswa ya ke da Ameen yana mamakin Umma. Ita kuma Surayya sai take ganin kamar Umma ta yi sanyi ne na d'an Lokaci. Saboda jiram su Sajida sai sha Biyu na rana suka tafi tashar Sharon suka yi gabadayan su, Mama bata samu zuwa ba diyar kanwarta ta rasu, Siyama ma bata je ba suna da Jarabawa. Sakeena ce kad'ai a dakin mama sai Sajida Sadiya, Sa'adatu bata samu zuwa ba wai mijinta ya hanata. Surayya sai su Goggo Hassu sai Hajiya Innani. Ba su isa ba sai karfe uku saura na Rana koda suka isa gidan suna ya Tumbatsa da Mutane. Gida cike fa, nan suka iske Saleema sun zo tun safe daman ta yi ta kiran su sukace suna hanya Saukar ban girma aka yi musu daman Tunda an sam suna hanya an tanadar musu nasu abincin na musammam. Shinkafa jallop da alala har da nama sai kunin aya da Zobo. Ni da kaina nazo har falo muka gaisa na kuma saka Ramatu da Safiya suka kai mu su yaran. Sun zo sun samu har anyaka Raguna Uku,har an gyara su ma tunda za'a soya da wuri a ba su nasu su tafi da shi. Sun sameni na yi kunshi sannan na yi kitso, kuma sun iske ni da wata Atamfa da muka yi anko da su Adda Fati har da Ramatu da Safiya. Na saka less ma da Safe Cikin kudin da Assadiq ya Turomin na siya. Sannan Maman suhailat ta bani materila na dinka shi shima. Sai Anty Surayya ta bani leda shake da kaya, akwai dinkakku da wad'anda ba'a dinka ba sai na jarirai da su pamparrs da sabulan wanka tace daga gare su ne. Turmin Atamfa yafi goma leshi guda Biyu har da mayafai da Hijabai, kayan yaran ma masu kyau da su fin kala goma, kuma damam an kara siya musu wasu, Ramatu da Safiya duk sun gwangwaje ya'yan na su da kayan yara har da takalma da safuna masu kyau. Su Adda na nuna mawa suna ta Godiya, taro ya yi armashi Sosai duka matan Baba saminu da na Baba Tanko duk sun zo min, su salima da la'asar suka dauki hanyar kaduna. Ita man jiki ta kawomin na yara Hajiya Murjanatu kuma ta aikomin da Atamfa da kayan yara Fathihatu kuma ta bani kudi. Kai hatta yan gidanmu ma samaru sun kawo sabulai, Ummi ma tazo ta kawomin kayan yara har Fadila sai gata tazo min suna tare da Ummin suka zo, na kuma san harda gulma ya kawota. Saboda gidan ya yi kad'an ga baki yasa Adda Fati ta Shiga makotan ta inda suke mutunci gidan maman hanna ta roka aka kai su Anty Surayya can suka kwana da Sassafe kuma aka tashi da aikin suya nama Saboda sun ce da wuri za su kama Hanya. Sai da Safen ne Sajida da Sadiya suka shiga har dakin da na ke Lokacin mun dawo wanka ni da Inna Talatu. Ita fita ta yi ta bamu waje, suka nemi gafarata nace musu ya wuce. Sannan suka bani wayata da Key din dakina tare da Atm din bankina. Sadiya ce ke sakin Fuska Sajida kuma tunda tace na yi hakuri ta kauda Fuska ni kuma na nuna musu komai ai ya wuce ni dai Tunda suka barni da dan'uwansu ai sun gama min komai. Misalin sha Biyu na rana suka tafi, Suka bar mim Innani kamar yadda Assadiq yace ta na ko kamkame da ya'yan magajin gida ta bakinta. Ta dankgwali Hancin wancan tace sulaimanu, sai ta dangwali hancin wancan tace muhammadu, ba ruwanta ita fa Imnani in za'a zauna ta yi ta Hira ba'a gwasaleta shikenan su Adda na shan Labaran su Assadiq da Abba. kuma ba sakaya komai da komai ta ke fad'a ni dai ina Ta tsoron kada ta je ta fad'i abunda ya faru tsakanina da su Sajida sai kuma aka ci sa'a Hirarta bai kaita can ba. An diba musu nama da yawa sun tafi da shi, Amma na Abba dabam na Assadiq ma dabam, sai kuma na Umma shima Dabam na su ne aka had'a waje d'aya. Naji dadin zuwan su kuma hakan ya kara tabbatar min da cewa da gaske ne Assadiq na sona kuma ya Tsayamin. Su Adda kuma suna ta Hiran sun fara Saukowa, suna ta kuma bani shawarwarin yadda zan kara jawo su gareni a sannu ko Saboda yan yaran nan. Ni dai jin su kawai na ke yi, zan yi dai iya bakin kokarina ammh ba lalle ne na Burge wasu daga cikin su ba. Ni dai na sakama raina zan zauna da Assadiq cikin Amana na yi masa Biyayya har karshen Rayuwata. Saboda ya yi min komai a Rayuwata ko nace ya na kan yi mini mana. *Janafty* *TMWB3K013* *TMW is a paid Novel, Pay 500 for regular or VIP N1K, Via 0552179550 Jamila Umar Gt bank, 09069067488* ‎Open this link to join my WhatsApp Group: https://chat.whatsapp.com/IhAz8h8nRy250ZnGGXwM65 Kamar yadda Umma ta fad'a ashe da gaske take yi, bayan suna da kwana uku ta shirya Sultana ta maidata gidan mijinta duk da sultanan na ta koke koken ita bazata koma ba sai ta gama Jarabawarta gabadaya Umma tace bata isa ba. Daga Sadiq har Abba suna mai Farincikin ganin Sauyawar Umma, Ko naman suna da yaji da su Anty Surayya suka kawo mata da girmamawa ta Karb'a ta na saka albarka su Sajida ma suna kokarin kawo mata wata mgana a gaban Surayya ta ja musu kunnen bata so, sannan ta na basu Umarnin su shirya da Dan'uwan su bata son ta kara jin wata mgana. A lokacin Sadiya sai ta kada baki tace"Umma mu kenan zamu bisa muna yi masa mgana! Yaron da ya fara gaba damu? Umma tace"Eh ku bi shi ku yi masa mgana ku basa hakuri, ai durkusa ma wada ba gajiyawa ba ne." Da haka ta kashe bakinsu kuma Sai suka yi girman kai ba su ba shi Hakurin ba, shi kuma bai kara bi ta kansu ba tunda dai Siya ta gayamasa sun je sun bata Hakuri kuma sun dawo mata da abunda suka karb'a. Umma bata nemi Rakiyar kowa ba sanda zata maida Sultana domin ko mutanem shinkafi tun jiya da Safe suka koma gidajensu Mama kuma tana gidan Gaisuwa. Sai da suka isa gidan ne ta saka Sultana ta zage itama ta tayata suka gyara gidan gabadaya ta kuma sakata ta Dauki waya ta kira Sadiq tace masa ta dawo tana Bukatar Cefane zata yi girki. A lokacin baki ta tura kafin tace"Umma ni fa baya kirana, ko mgana ma ba ya yi min indan ya ganni." Sai idanuwanta suka ciko da kwallah Tausayinta ya kama Umma sai dai bata nuna ba cikin ba ta Umarni tace"Maza ki kirasa, Umarni na ke baki ba shawara na zauna ina yi da ke ba." Dole kanwar naki ta kira Yaya Sadiq da ta manta rabon da su yi mgana ta waya. Kiran har ya katse bai dauka ba ta kalli Umma a marairaice tana fadin"Kin gani ko Umma bai Dauki Kirana ba, ni fa daman baya sona Hankalinsa na kan bazawarar matarsa da ta haifa masa ya'ya." Umma ta yi mata banza kamar bata ji ta ba, in da Sultana tasan yadda ta ke ji acikin ranta da bata kara harzuka ta ba. Duk lakwas din data ga tayi gani tayi Sadiq da Ubansa suna neman su saka Mahaifinta ya yi mata Mugun baki Saboda wata bakar Annoba, shiyasa ta yanke Shawaran gwara ta sauya taku. Ba abunda yafi bakanta mata rai sai ganin yadda Sadiq ke faman rawan kafa akan yarinyar nan da ya'yan da ta Haifa bashi kadai ba hadda Abban Siyama, sannan uwa uba ga Innani can ta je ta tare a gidan su yarinyar, shiyasa ta yanke shawaran gwara Sultana ta dawo da ita zata yi amfani ta fitar da yarinyar nan har Abada daga Rayuwar Sadiq tunda a baya ta kokarta bata samu nasara ba Sannan itama Sultanan ta samu ciki ta Haihu shime yanzu babban Burinta. Tana cikin wannan Tunanin har Sadiq ya Biyo bayan kiran Sultana muryan nasa a cunkushe kamar an yi masa Dole, yace wayar na silent ne bai ga kiranta ba sai daga baya. Itama cikin Dage baki ta gayamasa wai Umma tace ya siyo Cefane. Umma kamar ta maketa haka taji da Sauri ta karb'i wayar suka gaisa shi daman Abba ya fad'a masa Umma yau tace masa zata maida Sultana gidanta duk wannan Murnan da ya ke ji a baya na kasancewa da sultana ya kasa jinsa a wannan Lokacin. Shifa tunda ya Fahimci yarinyar bata da kunya ya gane ta su bazata taba zuwa d'aya ba kawai ta na cin Darajan masu daraja ne shiyasa Cikin Sauya mgana Umma tace"Kyale Sultana da Sakarci cewa tayi ta na so ta yi maka girki kuma ba Cefane sai nace to ta kiraka ta fad'a maka mana." Yana kwance ne yasa ya gyara kwanciyarsa yana fad'in"Shikenan Umma dame dame ake bukata sai na je a siyo? Cikin jin dadi Umma tace"Komai fa babu na Cefane, kuma kai da baka gama Jinya ba? Mirmishi kawai ya yi kafin yace"Na warke Umma, na ma kusa komawa aikina in sha Allahu." Jin haka yasa Umma ta fara yi masa addu'an tsarewa tare da Fatan nasara sun rabu tace anjuma yazo tana so ta yi mgana da shi tare da Sultana gabadaya yace mata toh. Kasala ce ta Rufesa a lokacin domin ba su jima da gama waya da Siya ba itama Gobe zata koma gidanta tare da Inna Talatu da zata Zauna da ita. Ya na Tunanin ya Tura mata itama kudin da za su yi Cefane duk da tace masa aikwai kayan abinci za su isa har yazo garin. Hakanan ya mike ya sauya kaya, yasan in bai je da kansa ba sai Umma ta rike sa a ransa. Saboda kafarsa da bata gama dawowa daidai ba, bai yo siyayyar da yawa ba kayan miya ya siya sai nama da kifi sai kayan lambu da Ruwa tare da lemu, kuma ba shi yaje ya kai ba Mallam tajudeen ya roka shi yaje ya kai ma su Umma sakon ya dawo. Umma da kanta ta taya Sultana girki mai rai da lafiya. Farar shinkafa da miyar naman Rago sai cowslow da suka had'a bayan sun gama ta saka Sultana ta tsala wanka da kwalliya ta na tashin kamshi. Umma ta yi ta kuranta da cewa ta yi kyau ita kuma Fuskar Sultana ba Fara'a. Dalilin da yasa Umma ta jata suka zauna bakin gado lokaci d'aya tana fadin"ko ke fa? Kin ganki kuwa? Sultana ta wani kara bata rai, sai Umma ta yi mirmishi kafin ta gyara zama tana fadin"Na lura in ban yi miki bayani ba, zaki iya bani matsala gashi ni kuma a yanzu ke ce Makamina." Cikin mamaki sultana tace"Bangane ba Umma? Umma ta gyara zama ta na kara Fuskantar Sultana Lokaci d'aya ta na fadin"Saboda Matar nan ta Sadiq bakar Annoba Mahaifina ke neman yi min baki, sun  kasa Fahimtar abunda na ke so su Fahimta a dole sai na saka ma auransa da wannan Shegiyar yarinya albarka ni kuma na Tsaneta kasancewarta ita da d'ana a waje daya matsala ne, Shiyasa na nuna musu na Hakura komai ya wuce, yanzu haka nace Sadiq ma zamu je Zariyan na yi barka naga yaran saboda su kara aminta dani. Ke kuma daga bangarenki ki yi amfani da kissa da kissina ki na y'a mace ki san yadda zaki yi ki hana ta jin Dadinsa har daga karshe ma ki Raba su, sannan kema ki yi kokarin ki samu Ciki ki haihu sai naga zuciyar wa zata kama saboda Ta haifi yan Biyu." Sultana ta yi shuru kafin tace"Kamar kin sani Umma, ni kaina yanzu bani da wani buri sai na ganin nima na Haihu kuma nima yan Biyu na ke son na Haifa Umma." Ta karishe kamar zata yi kuka, Umma tace"Da ikon Allah ke yan uku zaki Haifamana ita din banza, shiyasa na ke so ki kwantar da Hankalinki zamu rika waya ina tsara miki wasu abubuwan, ni yanzu in nace zan kara yin wani abu ido na kaina sai mgana ta kara zuwa kunnen mallam kuma ya yi min gargadi a ka sake kawo masa karana wlh sai ya bace ni fiye da Tunanina, ni kuma na samu Dakyar na kira shi na bashi Hakuri shiyasa ke na ke son ki natsu ki bar mganar zafin kishin nan ki Tsaya ki kwace shi daga wajenta." Sultana tace" anya Umma zan iyaa? Kina ganin yadda Yaya Sadiq baya ji kuma baya gani a kan matar nan fa." Idanuwamta suka tara kwallah ta Cigaba da fadin"Ita ya ke so, ni ai matar chuse ce ba ni da Daraja a wajensa." Umma tace"In ji waye? Yana sonki mana in da baya sonki da bai amince da auranki bayan ya aureta ba." Sultana ta kalli Umma cikin wani yanayi tace"Umma ni fa ina jin haushin ace itace gaba dani, Mayar kwacen miji kowa ai yasan Yaya Sadiq nawa ne ni kad'ai." Sai hawaye Umma na faman share mata ta na fadin"Kada wannan ya dameki ni a wajena bayan ke ba wata mata a gidan Sadiq, ki kwantar da Hankali da sannu zata fahimci karatun kurma." Da wad'anan kalaman Umma ta yi ta lallashin Sultana har ta samu ta yi shuru kuma ta yarda da Shawaran Umma. Sallar isha'i suka tashi suka yi, Abba ma ya yi mamakin da ya dawo gida ya iske bata dawo ba tana tare da Sultana har alokacin Da ya kirata cikin Dariya tace Sadiq ta ke jira yazo ta had'a su ta yi musu nasiha sannan sai ta taho. Shi har acikin ransa ya ke ganin Sauyawar Umma, tunda yasanta ko a baya da Tunani tare da hangen nesa kuma bai taba kamata da laifi irin wannan ba, shiyasa ta yi ta abubuwa shi kuma yana yi mata uzuri. Umma ta gaji da jiran Sadiq har wajen tara kuma tana so ta koma gida sai ta saka Sultana ta kara kiranshi sai yace yana kan hanya. Sanda ya shigo falon kallo d'aya ya yi ma Sultana ya kauda kansa ya maida wajen Umma. Ita kuma Umma ta hau take mata kafa Shiyasa ta mike ta isa gabansa tana yi masa sannu da zuwa. Ya kalleta sama sama sannan ya amsa yana karisawa kusa da Umma. Cikin Ladabi ya gaisheta, ta amsa cikin Fara'a ta na kara tambayansa kafarsa yace ta kusa warkewa gabadaya Tunda yanzu ya daina yawo da taimakon Sanda. Shine ma yake gayamata zai koma asibiti litini mai zuwa yaga likita. Umma tace yakamata yaje a kara ganinsa. Suna mganar nan Sultana taje ta kawo masa Ruwa Umma na ta faman mirmishi ta na fadin"ina ruwan Sultana." Shi dai kanzil bai ce ba ya dai Dauki Ruwan da ta zuba masa ya sha Saboda kada ya kwabe kokarinta a gaban Umma. Ganin Sultana zata shige Ciki kamar gaske Umma ta kirata ta dawo gabanta ta zauna. Umma ta gyara zama ta yi musu nasiha sosai, ita Sultana aka ce ta yi ma mijinta Biyayya. Sannan kada taji ya kawo kararta ta yi masa wani abu. Shi kuma akace ya yi adalci sannan ya san cewa Sultana Amanqce a wajensa in yaci Amanarta Allah na kallonsa. Cikin Tattausan lafazi ya kalli Umma kafin yace"Umma ni dai kinsan bani da matsala, diyarki ce ta ke da matsala ki gayamata rashin kunyar da ta koya daga baya bazan dauka ba, in tace bazata bari ba zamu yi ta samun matsala ne Umma." Da Sauri Umma tace"Kin ji ko? Ke sultana bashi hakuri." Ta fad'a ta na Hararan Sultana wacce ta sunkuyar da kanta Cikin yaukin baki tace"Kayi hakuri." Jinjina kai ya yi kafin yace"Na yi hakuri, sai mgana ta gaba Bazan lamunci ta rika aibatamin matata ba, in ita bata san darajan ta ba, ni na sani kuma ni zan zauna da su bisa Amana ne, kamar yadda bazan lamunci ita Siya ta aibatata ba, haka itama bazan taba bari ta aibatata ba." Umma ta jinjina kai kafin tace"Hakane, Sultana ki gyara don Allah? Ku zauna lafiya da junan ku tare da hakuri da juna." Kafin ta tafi sai da ta tabbatar da ta daidaita abunda ita ta yi silar lalacewarsa da kanta. Sadiq ya rakata har bakin Titi ta hau mashi zuwa gida Abba yaso ya Dauko mota Shi kuma yace sai yaje yaga likita ko zai fara amfani da Mota da kafarsa. Silar Umma yasa Sadiq ya Sauko ammh sai da Sultana ta kara sauke kai ta bashi Hakuri sannan ya hakura. Shi namiji ne da mace ta zame masa ginshiki kuma ya dad'e baya tare da mace shiyasa bai gwasale kokarin Sultana ba, bayan kuma tana da hakki a kansa da shima ya sauke shi a wannan Daran. Ita kuma abunda ke ranta itama ta yi tayi, ta samu ciki ta Haihu domin ta fi Hasiya samun matsayi a wajen Yaya Sadiq. Da kuma kissanta yasa har washegari bai fita ko'ina ba yana tare da Sultana sannan har yinin ranar bai kira Siya ba sai da ya fita sallar mangariba ya samu ya kirata suka yi mgana tace suna gida sun dawo tun da Rana ita da Inna talatu. Washegari kuma Big sis ta kirasa tace Umma ta kirata tun a jiya tace ta shirya zata rakata Zariya wajen Hasiya ta yi mata barka. Har acikin ransa yaji dadi da yaso yaje ammh ganin zai koma ganin likita yasa yace bari ya had'a gabadaya. Umma da Surayya suka tafi Zariya direban Abba kuma ya tukasu. Daman kuma Surayya sun yi mgana da Hasiya tace mata ta koma dakinta nan suka wuce kai Tsaye. ******** Tun kafin Anty Surayya ta kirani ta gayamin Umma na tafe Assadiq ya gayamin shiyasa na gayama Inna Talatu, Habiba tare da ita muka taho ita ta tashi ta dora girki. Wajajen azahar suka iso na yi wanka na Lokacin su Asim ma sun sha gayunsu suna tashin kamshi. Sai a ranar na taba gaida Umma ta amsa min cikin sakewa kad'an duk da bata washe min baki ba. Anty Surayya ta kwashi yaran ta zube mata a jikinta. Sai ga Umma ta kura musu ido ta na kallonsu, duk yadda ta so kada yaran su yi tasiri a ranta sai da suka yi. Farat d'aya taji sun bala'in Burgeta sun shiga cikin ranta da wani kauna. Tana kallonsu idanuwanta suka kawo kwallah ta kalli Surayya lokaci d'aya ta na fadin"Surayya yaran nan kamar magajin gida Lokacin yana karami." Surayya na dariya tace"Wlh nima haka nace Umma, sak Sadiq yana kamar su." Umma ta rumgumesu a jikinta tana saka musu albarka. Surayya ce ta waiga bata ga Innani ba shine ta yi mgana. Ina mirmishi nace"Tana dakin maman Suhailat makociyata." Inna talatu tace"Ta samu hira, maman suhailat akwai labarai a bakinta." Surayya tace"An had'u da an dace kenan" Muka yi dariya gabadayan mu, Habiba na aika ta kira Innanin sai gata da Sandarta da Uban gilashinta, jin muryansu Umma yasa ta washe baki ta na fadin"Salamatu kin huce kenan kin zo ganin jikokin naki? To wa ke fushi da yara? Balle yan Biyu kyautar Allah? Gwara da kika maida komai ba komai ba kin ji rayuwar nan ma nawa ta ke, yarinyar nan Hasiya da danginta duk mutanen kwarai ne, zaune na ke lafiya kamar ina cikin gidan sulaimanu." Umma dai sai ta sauya mganar ta hanyar gaida Innani. Surayya ma ta gaisheta ta amsa tana zama kan Kujera Lokaci daya tace"ina magajin gida? Umma tayi saurin cewa"Yana can kinsan sultana ta koma gidanta." Ta fad'a ta na satan kallona ni kuma ko a fuskata bata Fahimci wani abu ba. Duk da naji wani iri, ganin har yau da Safe mun yi mgana ammh bai Fadamin ba, wata zuciyar tace ina Ruwan ki Hasiya? Innani ta tabe baki kafin tace"Au ta gama koken koken iskancin nata ta koma kenan? Yarinyar haushi ta bani ni fa na ke mata mgana ta min banza yo, ni fa uwarta na haifa ba ita ba kuma Tunda taga ni nan na Saduda na bi Allah itama sai ta Saduda ta bi Allah da monzonsa, ohon mata dai ita ta sani, ke Surayya kiramin magajin gida na yi masa nasiha yana cewa yasan Allah ammh kuma baya adalci yarinyar nan ita da yaran nan suna Bukatarsa ammh ko keyarsa bamu gani ba, gwara shima dai yau na yi masa nasiha." Surayya na Danne dariyanta tace"Gaskiyarki Innani." Umma kuma sai ta kasa mgana Inna talatu ne ke fadin"Innani ko dai aiki ne ya yi masa yawa." Innani tace"Wani aiki? Ya warke ne da ya koma aikin nasa ban sani ba? Ta fad'a ta na kallon Surayya a Dage. Da Sauri Umma tace"Bai koma ba ammh yace min ya kusa komawa, kuma zai zo ganin likita litini mai zuwa inaga zai zo ya gansu Innani." Innani ta yi shuru kafin ta samu zarafin mgana Umma tace Surayya ta bama Hasiya ledan da suka zo da shi. Ledan Atamfofi ne guda uku sai kayan yara masu kyau da yarari na karb'a cikin murna ima nuna ma su Inna Talatu. Innani sai washe baki take yi tana fad'in"Lalle ana yi da wayan nan yaran." Umma dai bata biye mata ba, sallah suka yi sannan suka ci abinci Direba ma an kai masa nasa daga waje, Umma sai da Surayya tace Umma ta ijiye su Asim taci abinci sannan ta ba ma Inna talatu su, suna ta wasan su ba su da rigima da rana sai kukan Dare in daya ya fara daya zai kama sai asuba taimakona daya su inna Talatu ai da na raina kaina shiyasa ko kibar Jegon nan na kasa yi, sai dai cikar Haihuwa kawai da ya ragemin Rama na, sannan kumburin da na yi da Ciki har a lokacin kafafuwana ba su gama Saccewa. Karfe uku da wani abu suka tafi bayan sun yi sallar la'asar, Umma Kamar kada ta rabu da yaran haka nan take jin kaunarsu na ratsata kamar yaran su dawo wajenta da zama haka taji, innani kuma da Umma tace ko zata bisu su koma ne? Tace haka kurum ita ba ta tashi ba, a bari in tagaji da zama ita da kanta zata yi mgana, jin haka yasa Umma ta kama bakinta A mota ma Hiran yaran kawai Umma ke yi ma Surayya, ita kuma ta na Biye mata ganin da gaske yaran sun shiga zuciyar Umma ba da wasa ba. Haka da suka koma ta yi ta ma Abba mganarsu tana fadin kamar magajin gida yana karami. Abba yace shima yaga haka Lokacin da yaje asibiti ya gansu. Shifa sai gajiya ya yi ya koma yana kallon Umma yana Dariya a ransa tana ce masa kawai Sadiq ya bar Zariya nan ya Dauko matarsa tasa su dawo kusa da su da zama. Abba na dariya yace"Jikokin su dawo kusa da ke da zama dai zaki ce." Sai alokacin ta farga da abunda tace, Tsabar kaunar yara  ne yasa bata son su yi nesa da ita, ba ta ki a kullum ta rika ganin su ba. Sai ta yi shuru da bakinta Abba kuma yana jinjina ma Ubangiji mai kowa da kimai in ba'a yi wasa ba yaran nan sune Jarabatan Umma, tana kaunarsu kamar har sun fi Sadiq din matsayi yanzu acikin ranta. Har Sadiq sai da ya Fahimci haka, ta kirashi tana ta gayamssa yara nan kamar Shi yana karami kuma ta rika ce masa ya gayama matarsa ta kula da su  ta daina barin  su ba kayan Sanyi kada sanyi ya kamasu su Umma masu jikoki, kamar ba'a taba Haifa mata jika ba sai akan su. Ranar litini da Sadiq zai je ganin Likita dagacan ya Biya Zariya Tahir ya taho jiya da yammah zai Tukashi su tafi tare, Umma bar bakin mota ta bisu tana kara jaddada masa ya gaishe mata da Twins. Kamar tace zataje sai kuma ta fasa kada a Fahimci yanayinta. Ammh da yaran nan ta ke kwana acikin Ramta, ta na son su dawo kusa da ita ta riga ganinsu a koda yaushe. Sai da suka fara Zuwa asibitin sannan daganan suka dawo ta Zariya. Likita ya tabbatar da warkewa tare da Samun nasaran gyaran karaya, sannan yace masa zai iya cigaba da Tukinsa ba bu wata matsala. Sai dai Fatan Allah ya tsare kuma Nasara ma sosai aka samu ganin ko Dingishi Sadiq ba ya yi kafarsa da Hannunsa sambal suka warke. Sai dai tabbai in da ya samu Rauni ne mutum zai kallah ya Fahimci ya taba samun had'ari. Ko da suka iso wajena kamar ba Jego na ke yi ba mun cakare ni da su Asim, muka tarbi Babansu cikin Fara'a da Farinciki Tahir kuma shi ta su Asim kawai ya ke yi Har ya kalleni yana fadin"Kai girmansu ya bani mamaki fa." Ina dariya ban ce komai ba Assadiq ke fada masa suna shan har da madaran yara kuma basa wasa da Nono. Bayan sun gaisa da Inna talatu ta ba su waje ta koma dakin Maman suhailat ban da Innani da ta zauna ta rika musu Hira.. Karshenta dai nan muka barsu Tahir da yaran da ita muka Shiga ciki. Muna shiga ya Rumgumeni ya kamkameni yana shakan kamshin Jikina, mun jima a rike da juna Sannan ya sakeni ya koma ya na kallon Fuskata cikin Fara'a yace"Jegon nan ya yi miki kyau My siya." Mirmishi na yi kafin nace"Kai ne dalilin haka Abban Asim" Dariya ya saka yana fadin"Ehye wato na tashi daga Assadiq na koma Abban asim? Sai naji kunya na koma ina sunne kaina saman kirjinsa, shi kuma yana Biye min tare da Tsokana ta. Saboda za su tafi shiyasa bamu yi mgana sosai ba, na dai yi masa mganar zan je makaranta da ke kusa damu wata private zan kai musu Tp letter dina kafin su yi hutu tunda an kusa Fara jarabawa. Sannan mun yi mgana ko bayan na yi arba'in Habiba zata zauna dani har su Asim su fara wayau saboda ni kadai bazan iya ba, sai nace ya kira Adda Fati su yi mgana yace min zai kirata. Mun shagala aciki mun manta da kowa da komai. Assadiq ya Rud'e ya na ta kamani ni kuma ina kwace jikina Tunda jego na ke yi ga mikin aikin bai gama warkewa ba. Sai da Tahir ya rika kiransa a waya sannan ya sakeni ya fito ni kuma sai da na sako uban Hijabi Saboda kunya. Tahir dubu goma ya ba ni yace a siyama su Asim kayan wasa. Shi kuma Assadiq yace zai Turamin Sako ta waya da haka muka yi sallama. Cikin ikon Allah Innani tace zata bisu da na ce har kin gaji damu? Sai tace"Ina fa, kawai dai naga kamar ban kyauta ba ne, sulaimanu ma na da Hakki a kaina. Kada ransa ya baci yaga nazo nan na tare, gwara dai na koma shima ya ganni hankalinsa ya kwanta kada kuma na yi rashin Adalci." Ni kaina sai da na yi Dariya Assadiq ne kawai ya Murmusa. Tahir kuma har yana rike ciki, Inna talatu ta yi cewa zata yi kewar Innani, sai ga Innani na kuka ta na fadin"Ni kaina ba'a son raina zan tafi ba, sulaimanu na ke tausayi." Sai kuma ta koma kallonsu Asim ganinsu ya sa ta kara kecewa da kuka ta na fadin"Yaran nan abun Tausayi uwarsu kadai ke wahala da su, Ubansu bai san wahalan ya'ya ba." Assadiq ya kalleta kafin yace"Sai ke kika san wahalan na su ko? Innani ta ballamasa harara kafin tace"Kwarai nan yara nan ke tsala kukan dare haka muke hana idanuwan mu barci muna wahalan reno, ammh daga karshe baka Gode ba." Karamin Tsaki kawai ya yi ya fice daga dakin ya bar Tahir na Dariya. Innani ta kwabe baki kafin tace"Masifaffe duk ya zama wani mafad'aci yo ni ko ubansa Sulaimanu lallabani ya ke yi Ehe." Naji dadin zamana da innani a wajena na bata atamfa da sabulan wanka da omo har da Turare ta yi ta min godiya ta a sakamin albarka. tace kuma kada na damu zata dawo daman domin tana jin Tausayin sulaimanu in ba haka ba inda zataje nan zata zauna tare da yara nan ta na tayani renon su. Har Habiba sai da tace gidan ba Dadi da Innani ta tafi, innani ai akwai hiran ban dariya. Farida sai dai ta koma bangaran Umma, Shiyasa da Innani ta dawo ta yi ta Murna, innani tace shaf ta manta da Amana a hannunta to gaba kafarta kafar Farida bazata barta anan ba, ba mai Tausayin da zai kula da ita. Ba wanda yace mata a'a sanin halinta kada ayi mgana ta tada kukanta na Fama sai aka bita da yadda take so. ******** Bayan wata d'aya." Kwana uku da yin Arba'in din su Asim Safiya ta zo ta goyamin Asif ni kuma na goya Asim mukaje private school d'in da ke kusa damu na kai musu T.p letter a lokacin ma suna Wassanin yara ne sun gama Jarabawa hutu za su ba da. Na gaya musu tsaikon da na samu aiki aka yi na haihu ganin yaran yasa suka karbeni suka bani accpted letter wanda zan kai makaranta suka ce bayan an dawo hutu sai na fara zuwa.. Jin dadina da Safiya tace ba'a fara zuwa Dubawa ba, makaranta ne na sha Fad'a a Tp office sai da suka ga su Asim sannan suka yarda da uzurina. Tunda na yi arba'in Inna Talatu kwana daya kawai ta kara ta koma gida, na bata atamfofi guda Biyu Assadiq ma ya siya mata har da waya tunda a gidana na hannunta ta lalace sannan ya bata kudi, muka rabu tana min godiya mu ma muna yi mata. Habiba ce ke wajena Tunda Assadiq ya yi mgana da Add Fati ta amince daganan na ke bata kudin mota ta na tafiya makaranta. Assadiq ya koma Abuja wajen aikinsa sannan kuma Abba ya gwangwajesa da Sabuwar Mota Camry mai ruwan madara ta yi kyau motar tunda har nan yazo min da ita mun shiga ni da su Asim mun je yawo. Yawon arba'in na fara nan cikin gari tunda yace min har wajen Amma zai kaini mu kai mata su Asim in ya dawo sannan zamu je gusau mu yi kwanaki Umma ta matsa yaushe zan kai mata su Asim? Umma ce ta bani mamaki har waya muna yi da ita, in yau bata kirani ba gobe zata kirani ta ji ya ya lafiyar su Asim har wasanninsu ina kara mata tana ji. Ni yanzu Hankalina duk ya kwanta, in da nake hangen matsala Cikin ikon Allah komai ya zo ya zama kamar bai Faru ba. Naje gidan Adda Fati na kwana daya, Gidan Ramatu ma na kwana ita kwana muka yi mganar kayan gyaran jiki nace mata Adda Rukayya tace akwai wata marubuciyar littafan Hausa kayanta na da kyau da inganci. Ramatu tace in na samu na gayamata itama zata siya ammh sai ta Haihu Tunda Tsohon ciki gareta. Gidan Adda Rukkaya ne da naje ban kwana ba saboda mijinta na dai yini da ita kuma ta kiramin mai saida kayan gyaran Gudiyo kaya masu inganci daga Chadi. Surayya Dee marubuciyar Littafin Halinyau, sabo da kaza da kuma bakar Ta'ada, ashe Adda Rukayya tana karanta littafanta ta nan suka saba yanzu kuma suna cinikayar kayan gyara da ita. Ta kirata a gabana ta fad'a mata na haihu kuma duk da aiki aka yi min ina so na yi gyara nan take tace zata had'amin komai da komai cikin Farashi mai Sauki zata sauko a mota zuwa Jibi Nima ban yi kasa a gwiwaba na tura ma Adda Rukayya kudin na kuma karbi Lambarta Tunda nace mata Ramatu ma tana so zata siya. +234 803 277 3332 Washegari Samaru Habiba ta rakani har Gidan da muka zauna na kai musu su Asim su maman Boy dai ana nan jiya i yau ba wani Cigaban Rayuwa. Na jima a gidan suna ina suka sakani sai da  muka yi la'asar muka fito. A hanya na had'u da wata kanwar Salisu ta na ta kallona ganin haka yasa na gaisheta. Ta amsa ganina da goyo tare da Habiba yasa tace ko na haihu ne? Habiba ce ta ce mata Eh,Har kuma yaran na Bude mata ta gani ta yi musu addu'a har muka kule tana waigen mu. A ranar naje Dirimi gidan Baba Tanko da Baba Saminu, na gaishe su tare da kai musu su Asim. Baba Tanko har Daukansu ya yi sannan ya kalleni yana fadin"kwanaki naji an ce dangin mijin naki sun miki koran kare? Ban yi mamakin jin ya samu Labari ba, na san kuma daga bakin Baba Jibril yaji kila shima Salima ta fitar da mganar waje. Shiyasa na yi masa Mirmishi nace"Ai komai ya wuce yanzu in sha Allahu." Kamar  dai ba haka ya so ba, Sai dai bai kara mgana ba, ban wani jima ba daganan na biya gidan Goggon kona muka gaisa ita kam sai faman bugun Ruwan cikina ta ke yi taji halin da na ke ciki da yan'uwan mijina ni kuma ina ce mata komai lafiya. To ai taga haka dagani har ya'yana muna cikin kama mai kyau ba ma cikin wahala. Sai da na tabbatar da naje gidaajensu na gaishe su kamar yadda Amma ta bani umarni, har gidan su Safiya naje na yinin mata, Domin ai Safiya kawar Amanace sannan ta zauna a gida na fara shan mganin gyarana da akq aikomin daga kano. Tunda a satin Assadiq yace min wajena zai sauka sai faman rawan jiki ya ke yi min nasan kuma ba sauki Shiyasa na dagee ina ta amfani da mungunanan kuma naji dadin su sosai. Kafin ramar jumma'a sai da na tabbatar da nayi zam, ni kaina naji ina son kasancewa da mijina da yammah ya iso, Habiba da rana ta koma gidan Adda Fati ammh kafin ta tafi sai da ta tayani aiki na yi masa girke girke masu dadi da lemuka. Tuwon shinkafa miyar a gushi da Tokfish, da ganda sai zobo da kunin Aya. Allah yasa yau su Asim naji abun arziki ba su yi min rigima ba Tunda na yi musu wanka suka ji ruwan zafi sai barci. Har ya dawo ba su tashi har sai da ya yi wanka ya ci abinci sannan ya tada su da kanshi yana yi musu wasa. Yara nan kamar su san babansu ya Dawo ba su yi mana kukan dare ba. Suka bar Babansu ya sha Shagali. Da asuba ne suka fara kuka sai na Dauke Asim na fara bashi Nono shi kuma sai ya Dauki Asif yana lallashinsa. Ni ce ina dariya nace"Yara nan sun bani mamaki, ko kukan daren da suka saba mana yau ba su yi ba." Na tuna ranar da ma kai su allura irin kukan da suka kwana suna yi mana. Mirmishi ya yi kafin yace"Yaran albarka kenan, baza su takurama Abban su ba" Yaso ranar muje gaida Amma, ammh sai na rokeshi in ya kaimu ya barni na kwana biyu a wajenta shiyasa sai ya bari sai Ranar litini ya kaini daganan ya wuce Abuja. In na gama kwanakina sai na dawo, kuma hakan ce ta faru weekend din nan tare muka yi shi, ni da mijina da ya'yana. Shi ya ke tayani Renonsu kamar kada ya tafi, ina jinsu wani Lokacin suna waya da Sultana, ni ma kuma ina waya da su Anty Surayya Anty Saddiqa da Saliha. Sai Anty Sa'ima da Umma da tafi kowa kirana yanzu Saboda Darajan su Asim. Muna hanyar zuwa wajen Amma ya ke fad'amin yaushe ya kamata na Shirya tafiya gusau.? nace masa kafin dai a koma makaranta Saboda Tp na Sai yace wannan ba matsala  ba ne sati daya dai ai bazai zama abun damuwa ba. Mun isa da wuri tunda da safe muka kama Hanya Suprise na yi ma Amma sai dai kawai ta ganmu kamar daga sama. Ta yi murna sosai ta rasa ina zata sakamu Saboda Farinciki, Barin ma Assadiq da ta rika yi masa barka da arziki. Shima dalilin yi mata gaisuwan Adda yasa ya zo, sannan da kuma kawo mu ni da yara bai wani jima ba ruwa kawai ya sha ko lemun da Hamma Isuhu ya kawo masa bai sha ba. Ya yi ma Amma gaisuwa tare sallama sannan ya tafi, 10k ya ba ma Amma ta yi ta godiya ita ai ganina cikin Farinciki ya isheta komai. Na rakasa har mota su Asim na barci sai dai ya yi musu Rumguma daya bayan daya da Sumbata. Nima haka ya rumgumeni ya sumbaceni cikin kauna kafin mu yi sallama da cewa sai mun yi waya. Daganan Abuja ya wuce tunda Hanya ce. Ni kuma ya barni wajen Amma ta da naji kamar an sakani a cikin aljannah. Amma tunda muka zo ita ke wahala da su Asim Allah sarki sai fadi take yi"Allah ya sa ina raye gashi ina Goya ya'yan Hasiyata a bayana. Allah ya jikan Adda ta sha fad'amin kema watarana zaki ji dadin aure kamar kowata mace." Sai ga Amma na hawaye sai na koma lallashinta. Na zo mata da Sabulan wanka da na wanki da su omo sannan cikin kayan sunan da na samu na kawo mata leshi daya da Atamfa. Amma na ta godiya tana kara godema Allah Hasiya ma ta samu Farincikin da ta ke mata fata. Kwana Biyar na yi a wajen Amma sannan Hamma Isuhu ya kaini tasha ya sakani a motar zariya. Ina mota ina Tunanin Hirar mu da Amma, ni na bata labarin irin yadda Umman Assadiq ta ke kirana saboda su Asim sannan yanzu ma ta matsa sai na je gusau. Ammh tace na shirya naje, Sannan daman ta jima tana kai kukanta ga Allah, akan Allah ya dora kaunata a zukatan yan'uwan mijina ko Saboda Darajan yaran nan kuma tana ji a jikinta Allah nee ya amshi addu'arta. Ta bani shawaran na yi hakuri na maida kaina wajen biyayya ga Mijina, sannan na bi yan'uwansa sau da kafa sannan in zan je na je musu da wani abun saboda alheri da kyautatawa na da dad'i. Da wannan na fara Tunanin abunda zan kai ma Umma da Abba ga Innani ga Mama, Amma tace har Sultana in naje na yi mata alheri bakomai taci Darajan Abubakar. Washegarin ranar da na dawo Assadiq ya kirani yace min yau gusau zai je, saboda haka na shirya sati mai zuwa zai zo ya Daukeni zuwa Gusau achan sai barni na yi koda sati daya ne Ban yi musu ba nace Allah ya kaimu, daman tunani makaranta ne, sai kuma na lissafi naga a satin ne za'a koma zan iya zuwa na dawo kafin karatu ya kamkama. ****** Gusau. Kamar yadda ya fad'ama Hasiya Ranar jumma'a ya baro Abuja zuwa Gusai, Ya samu kyakyawan Tarba wajen Sultana kamar yadda ta nuna ta sauya shima sai ya nuna mata ta na da fa da matsayi itama a rayuwarsa. Cikin Farimciki suka kwana da Safe tare da ita suka je gaida su Umma suka dawo kuma tare. Abunda ya lura ta rage fara'a saboda tun suna falon Umma da taji Umma na tambayan yaushe Twins za su zo mata ne taji shuru, yace sati mai zuwa zai je ya Daukosu Umma ta fara washe baki tana fara'a. Abunda ya bama sultana Haushi Umma yanzu hankalinta na kan ya'yan da tace ba ta so, ammh yanzu ita ko damuwa da ita bata yi, har complain taje ta yi mata da cewa ko za su je asibiti ne ciki har yanzu ita bata samu ba, Umma tace wai ta kara Hakuri yaushe duka duka ta koma? Sai kuma daman su Anty Sajida suna gayamata Umma yanzu son ya'yan nan ya Rufe mata ido bata ganin bakin Hasiya yanzu ta ma daina Zaginta. Shiyasa tunda suka dawo ta ke masa cin mgana shi kuma sai ya kyaleta bai biye mata ba, shi ke janta ma da Hira ta na wani basarwa. Sai da rana da ta yi musu abinci tunda yanzu tana gida sun gama jarabawa. Suna kan Dining suna cin abinci ya kalleta yana fad'in" Siya zata zo kawo ma su Umma  yaran nan su Asim saboda haka zata sauka anan Acikin dakunan ki.  ki zab'a mata guda dayan da zata sauka aciki." Cikin Mamaki sultana ta kallesa kafin tace"Nan gidan wai ka ke nufi? Cikin shima mamakin tambayarta ya kura mata ido kafin yace"Eh nan gidan na ke mgana, ko ina da wani gidan da ya wuce nan ne" Sultana ta tura bakinta gaba kafin tace"Tabdijam ni ai bani da masaukinta a gidana." Hancinsa a bude yace"Bangane ba? Gidan ki naji kin ce? Kai Tsaye sultana tace"Eh mana tunda ai saboda ni Abba ya baka kyautar gidan saboda haka da gidan da abunda ke cikin gidan duka mallakina ne" Tsabar mamaki ya hana Sadiq mgana, kallon Sultana ya ke yi yana kara jinjina karfin halinta. Cikin dan mirmishi yace"Oh ko Mallam shitu ne ya siya miki gidan sai kika taimakamin na ke zaune nima aciki? Sultana bata taba tunanin irin amsar da zata fito daga bakin Yaya Sadiq ba kenan. Cikin mamaki tace"Ni? Mahaifina ka ke zagi Yaya Sadiq a kan wata banzar bazawar..! Bata karisa ba taga ya mike da sauri ta matsa baya. Shi kuma da hannu ya nunata yana fad'in"Kul din ki, kin manta kashedin da na yi miki a gaban Umma? Da gaske na ke bazan dauki reni ko zagin cin mutumcin matata ba, baki isa ba ta na gaba da ke awajena ita na fara aura kafin na aure ki to ya kamata koyi  girmamata, ya rage naki ki kiyaye ko karki kiyaye ni dai nace miki kul d'in ki yarinya." Kawai sai Sultana ta fashe da kuka ta na fadin"Yanzu ni kayi ma gorin gida saboda matarka? Saboda ka fi sonta dani shiyasa ka kira sunan Ubana kai tsaye ba ka ji kunyar haka ba." Yana jinta ammh yasan in ya Biye mata za'a iya yin mara kyau..shiyasa ya mike daga kan Dining din, ko abincin bai gama ci ba ya kama hanyar fita daga Falon lokaci d'aya yana fadin"In kin daukeshi a matsayin gorin to bazan ce miki ba haka ba ne sultana, gorin ne" Yana jiyo kukanta ya yi kamar bai ji ba daman da key din motarsa a jikinsa ya shige motarsa ya bar mata gidan. Gidan Big sis yaje suka sha Hiransu, yana gayamata zuwan Siya tare da su Asim. Surraya tace"Kace Umma zata yi sallarta kenan." Yana dariya yace"Umma na son yaran nan fa, ni fa ina ganin su za su kwace sunan magajin gida." Surayya ta saka Dariya lokaci daya tana Fadin"Umma ai ina tsoron Allah ne ya fara kamata saura su Sajida." A gidanta ya ci abinci ya koshi shima har mangariba sallah kawai ke fita da shi. Ya baro gidanta kenan bai ko biya ta gidan Su Umma ba ya sauka a gidansa ya wuce sai ya tarar Sultana bata gida. Da ya tambayi megadi sai ya gayamasa yana fita ba dadewa itama ta fita. Sai ya kada kai yasan kila tana gidan wajen Umma, sai dai yana zuwa Shashen Umma ya ga bai ganta ba. Sai ya tambayi Umma. Ita kuma cikin mamaki ta kallesa kafin tace"Au ba ta koma gida ba? Cikin mamaki ya ke kallo Umma kafin ya yi mgana ta cigaba da fad'in" Tazo min nan da rana haka tana min kukan wai kace Matarka a gidanta zata sauka don tace gidanta ne wai shine ka yi mata gorin gida ka kuma kira sunan mahaifinta ka zaga." Cikin dage gira yace"Ita sultanan tace haka? Umma tace"Eh ni dai na bata hakuri nace gidanka ne kana da ikon zabar inda Matarka zata sauka, to ta dai fita ni wlh na dauka gida ta tafi." Sadiq ya yi huci kawai bai yi mgana kafin ya mike yana fadin"Umma ki kyaleta ina tunanin tana gidan su" Umma tace"Bari dai na kira ta naji." Nan take Umma ta hau kiran Sultana ammh sai taki Dauka. Sai ta kira mallam Shitu bayan ya Dauka sun gaisa ta tambayeshi Ko Sultana tazo? Cikin bacin rai yace"Ta zo shashshan yarinya Butulu, tazo min da wata mganar banza na Fattaketa nace komai Dare bazata kwanamin a gida ba, kuma in bata kwana gidan mijinta bq sai na ci mutumcinta." Umma sai ta fara bashi Hakuri cikin jin kunya yace shi ya kamata ya basu hakuri yarinya tana neman gagaransu. Su da suka riketa suka yi mata komai a Rayuwa. Sadiq bai jira Umma ta gama waya ba ya fice bai shiga bangaren Abba ba, saboda Mama na wajensa sai kawai ya Shiga mota ya wuce gida ammh ya Tsaya a masallaci sallar isha'i. Ya na komawa gida megadi yace masa Hajiya ta dawo sai ya gyad'a kai. Yana Shiga ya ganta zaune a falo ta na kuka. Ya dad'e tsaye yana kallonta kafin kawai ya kad'a kai ya wuce cikin Dakinsa. A ransa yana jin bazai lallasheta ba Tunda shi dai bai yi mata wani abu ba, itace ta dauki Lamarin da Zafi. *Janafty* *TMWB3K014* *TMW is a paid Novel, Pay 500 for regular or VIP N1K, Via 0552179550 Jamila Umar Gt bank, 09069067488* https://chat.whatsapp.com/IhAz8h8nRy250ZnGGXwM65 *BOJUWA HERBAL'S BY SURAYYA DEE*! *Akwai kaya masu kyau a cikin farashi mai sauki* *Saiwowin maganin sanyi* *Saiwowin Tsumi* *Saiwowin dahuwar kaza* *Saiwowin dahuwar tattabaru* *Gumba* *Tsumin kwakwa* *Y'aya'n gadali* *Hadadden daka*. *Tsugunno mai sa a matse* *Goran tula* *Goran tula syrup* *Garin goran tula*. *Maganin gyaran nono*. *Zuma ta mussaman*. *Tsumi*. *Gaban ayu*. *Hakkin daka gangariya*. *Da sauran kayayyaki na mussaman da basu da illah*. *Domin kuwa asalin Saiwowin ne da ake kawo su daga Chad*. *Abu mai kyau shi ke siyar da kansa ku tuntube ni dan samun naku kayan cikin sauki da mututantawa. Ina aikawa ko ina a fad'in tarairaiyar Nijeriya* *08032773332* *Ana dafa GIMBIYAR KAZA da tattabarun garari*. Kwanciyarsa ya yi, ko abinci bai Nema ba tunda ya ciko cikinsa a gidan Big sis ba shi da damuwa. Shi abun na Sultana yanzu ya daina mamakinta in ta yi wani abun. A baya yana kallon wani abun in tayi a matsayin yarinta sannan ya na yi mata uzuri ashe ba haka ba ne ta girmi Tunaninshi. Yana nan kwance sai ga kiran mallam shitu, sai a lokacin yaji yar kunyar sunan da ya kama nashi kai tsaye duk da bai daukesa gori ko cin zarafi ba. Cikin jin nauyi ya dauka suka gaisa kamar yadda suka saba, mallam Shitu ya tambaye shi ko Sultana ta dawo? sai Sadiq yace gata can a falo. Mallam Shitu ya cigaba da fad'in"Ka yi hakuri Abubakar, sai dai zan baka Umarnin duk wani shegentaka da yarinyar nan zata kawo maka ka yi mata Hukunci daidai da abunda ta aikata Tunda bata da kirki, shashasha ce." Sadiq yace"Bakomai Mallam, Yarinta ke damunta zata bari in ta kara mallakan Hankalin kanta." Mallam Shitu yace"Wani hankali? Yarinyar da ta wuce ashirin ka ke kira yarinya? Kanenta ga su nan ai baza su aikata irin sakarcinta ba. Nan ta zo ta na gayamin wasu sakarcin mganganu ban Saurareta ba na Fattaketa ko zama ban bari ta yi ba." Sadiq ya sauke ajiyar zuciya kafin yace"Kuma ni duk abunda tace na yi mata ba gaskiya ba ne, ina iya bakin kokarina wajen kwatatan adalci a Tsakaninsu." Mallam Shitu yace"Haba ai ba sai ka Fad'a ba kowa ya san komai, ni ban saurareta ba kai ma ina baka Umarni in ta kawo maka wani shegentaka ka yi mganinta." Da haka sukayi sallama, ya kwanta ya yi shuru yana tunanin Rayuwa. Tabbas ijiye mace Fiye da d'aya ba abu ba ne mai sauki. Ita Sultana duk bata ga abunda ya ke yi ba, ba zata taba godema kokarinsa ba. Rayuwa yanzu ta yi tsada ko man da ya ke konawa wajen jeka ka dawo tsakanin gusau da Zariya kad'ai ya ishesa. Kada ma a saka Labarin sauran Hidimdimunsa da na su da ke kansa, duk ita bata gode ba sai kokarin tada rigima take yi, shi kuma Saboda Darajan su Umma yasa bazai Biye mata ba. Sultaana kuwa har kara jiniyan kukanta ta ke yi a tunaninta ko Yaya Sadiq zai fito ya duba ta ya lallasheta. Sai dai hakkanta bai cinma ruwa ba, har ta gaji da daga murya ta koma ta na kukan zucci. Abu daya yafi bata mata rai yadda Umma taki goya mata baya kiri kiri tace wai ta koma ta yi hakuri ta bar Yaya Sadiq ya sauki bazawarar matarsa a gidanta ai hakan ba adalci ba ne. Shiyasa batare da shawara da kowa ba ta kama hanya sai shinkafi. Ai ko ta na zuwa sai da ta yi nadamar zuwa ko kad'an babanta bai Saurareta ba, balle yaji irin abunda aka yi mata ko minti talatin bai bari tayi a gidan ba ya fattaketa ya na kiranta butulu Tunda har zata zo ta na kawo mganar wad'anda suka riketa suka Rufama Rayuwarta asiri. Ko ruwa bai bari ta sha ba yace ta koma Gidan mijinta, sannan kuma kada ta kawo dawo masa gida matukar ba alheri ya kawo ta ba. Kukan da take yi duk rabinsa na kishi ne, bakinciki take yi da Hasiya ganin har tazo ta haihu kuma ga shi kamar Umma ta fara son yaran nan..shiyasa yanzu ido rufe ta ke so tayi Ciki itama yan Biyu ko Umma zata Daina son yaran nan. Saboda jin Hauahinsa a d'ayan bedroom d'inta ta kwana, da Safe kuma ta yi kwanciyar ba ta yi abun karyawa ba Sadiq ko bai ko Tsaya ba ballatana ya wulakanta Da kansa ya shiga kitchen ya Dafa Ruwan zafi sannan ya soya kawai yazo ya had'a Tea ya sha da Kwai tare da Buredi. Yaso ya kai gobe da Safe ammh ganin iskancin Sultana yasa ya yi shirin komawa Abuja a ranar. Bayan ya gama karyawa ya koma daki ya kira Siya suka yi ta waya suna shan Soyayyarsu sai sha Biyu ya tashi ya yi wanka ya shirya ya Dauki Mota ya fita daga masallaci ya shiga gida ya gaida su Umma, Ko alokacin sai da Umma ta kara tambayarsa Yaushe su Asim za su zo? Yace sati mai zuwa. Sai ga Umma cikin Fara'a ta na fad'in"Ma sha Allah, ammh za su kwana Biyu ko? Kai Tsaye yace"Eh sati nace za su yi, ko ba na nan sai direban Abba ya maidata gida tunda ga yara." Umma tace"Eh hakane kam," Suka yi shuru na wani lokaci shi yana Duba wayarsa ne. Tahir ne ya ga kwana Biyun nan gabadaya in dai ba abun siyasa ba gabadaya post dinsa na Soyayya ne, to ya fara zargin wannan karon Tahir ya fara soyayya gaskiya ya daina yaudaran ya'yan mutane. Hankalinsa na kan wayarsa yaji Umma na tambayarsa can gidan Siya zata sauka in ta zo kenan? Sai ya maida wayarsa aljihu Lokaci daya ya na kallonta kafin yace"Eh haka nace Umma, tunda ina da gida bai kamata ta rika sauka gidan big sis ba." Umma ta jinjina kai a zuciyarta kamar tace to ta sauka a waje na  mana Saboda su Asim ammh sai ta kasa mgana shi kuma ganin haka yasa ya kara kallonta yana fad'in"Ko hakan bai yi ba Umma? Da Sauri tace"Ah ya yi sosai ma, Allah ya kawo su dai lafiya." Ya amsa da Ameen Ameen daganan yace mata yau zai tafi, bata masa mganar Sultana ba sai da taji yau zai koma cikin mamaki tace"Yau kuma? Sultanan bata dawo ba ne? A dakune yace"Ta dawo mana, ina da ayyuka a office ne gobe da Safe." Nan dai ta yi masa Fatan alheri ya sallameta daganan ya shiga bangaren Mama ya kara yi mata gaisuwa duk da har gidan gaisuwan yaje. Daganan da ya fito sai ya shiga bangaren Innani ya iske ta tare da Farida da Siyama suka gaisheshi. Innani na ganinsa ta washe baki ta na yi masa kirarin baban yan Biyu. Bai jima a wajenta ba ya yi mata sallama ta shiga kwarara masa addu'a tun ballatana ma da ya bata kudi. Yana jinta yan Biyu da mamansu sun sha addu'o'i. Abba baya nan sai dai ya kirasa ta waya, Umma ce ta kirasa tace in bai tafi ba ya dawo tana son ganinsa. Da sauri ya koma bangarenta ta na zaune inda ya barta. Shima sai ya koma ya zauna inda ya taahi Lokaci d'aya yana fad'in"Umma lafiya kuwa? Kai Tsaye Umma tace"Daman saboda na yi maka mgana ne, kana ganin bai kamata matarka ta can zariya ta dawo nan da zama ba? Gani na yi kai ma ya kamata ka Huta zirga zirgan zai yi maka yawa kaje can kazo nan." Sadiq ya yi shuru kafin yace"Zata dawo Umma, ammh ba yanzu ba." Cikin mamakinsa Umma tace"Bangane ba? To meyasa? Kai Tsaye yace"Saboda ta na karatu, ammh ta kusa gamawa, nima ina Tunanin in tagama ta dawo nan da zama ko can inda na ke aiki." Umma da sauri tace"A'a ba can ba, nan din dai, in can ka ke so sai dai ka tafi da sultana." Kallon Umma ya yi, sai dai bai yi mgana ba kad'a kai kawai ya yi kafin yace"to Umma shikenan." Ita kuma tace hakane saboda bata son su Asim din su yi nesa da ita. In suka koma Abuja ai sai ta Dade bata gansu ba, kuma yanzu yadda take kaunar yaran nan bata jin ko iyayensu suna da iko a kansu yadda take jin tana da shi. Daganan Shima gida ya koma sai dai yana ta auna mganar Umma, ya Fahimceta Saboda su Asim ne, shima kuma yana Tunanin haka Siya ta fara zama Gusau in ya samu Ma'aikatansu sun saka hannu a takardan ba su Loan gida da Mota shi sai ya karb'i na gida duk wata za'a rika cirewa a albashinsa. Gwara dai ya fara natsuwa waje daya shi kanshi ya gaji da duk bayan sati yana Hanyar Zariya ko hanyar Gusau. Ya kamata ya natsu waje daya ko shima ya samu cikakiyar natsuwar da ya ke fata. Har daki ya bi Sultana ya yi mata sallama ta na kwance, ko dago kai batayi ba ta amsa masa kamar bata son ta yi mgana. Shi kuma bai damu kansa ba ya ijiye mata kud'i saman Side drower d'in gadon da ta ke kwance ya ficewarsa lokaci daya yana girgiza kansa, shi a tarihin zamansa da Siya ba tab'a masa irin wannan ba, shi fa a zamantewarsa da Siya sai dai shi ya ji kunya in ya yi mata laifi ammh ita bata taba yi masa laifin da yaji ta bata masa rai ba. Sai dai abunda ba'a rasa ba, na zamantakewar yau da gobe. Share Tunaninta ya yi saboda Tuki zai yi kada taje Tunanin ya yi masa ya kara samun matsala. Kafin ya tashi sai da ya kira Siya ya gayamata zai kama hanyar Abuja cikin yanayin mganarta tace"Assadiq yau da rana kuma zaka tafi? Kai Tsaye yace"Zan shiga Office da wuri ne Siyata." Bata damu sai ta kara jin wani Dalili ba, ta shiga yi masa addu'an fatan isa lafiya har ta na kara masa gwarancin su Asim. Kafin su yi sallama haka ya Dauki hanya cikin Farinciki tuni ya shafe Tunanin Sultana ballatana Sakarcinta. Sai bayan mangriba ya isa Abuja Abba ya yi ta kiransa yana hanya sai da bayan ya natsa ya yi sallah yaci abinci sannan ya kira shi suka yi mgana. Bayan nan ya kira Siya ya gayamata ya isa, itama ta na ta kiranshi yace bai Sauka ba. Umma kuma daman tana tare da Abba domin yaji muryanta Lokacin da suke waya. Sultana ma ya kirata Saboda ya fita hakkinta kira Biyu sai ana uku ta Dauka tana wani cin mgana shi dai bai Tsaya nuna ya gane fushi ta ke yi ba yace mata ya isa lafiya. Kawai Ok tace ta kashe wayarta sai ya yi Sororo a fili ya Furta"Yarinyar nan ta yi nisa." Danne bacin ransa kawai ya yi saboda hakane ma sai kawai ya Kira Tahir ai sai yaji Tahir na amfani da wayar. sabodq yakuresa yasa ya yi ta kara kiransa wajen sau biyar duk bai gama wayar ba, wajen awa daya sannan sai gashi ya Biyo kiran Sadiq din yana Dauka yace"Wai lafiya ka ke ta min kira ba daga kafa? Sadiq yace"Allah ya baka Hakuri ai bansan ka fara Serious Soyayya ba ne." Sai Tahir ya yi shuru bai yi mgana ba, Sadiq ya sha Mur kafin yace"Ina taya ka Murna, sannan barka iyayen yara za su huta da tsabar yaudaran musu ya'ya da ka dinga yi a baya." Tahir ya yi dariya kafin yace"To nagode, kasan komai Time ne nima ina ji a jikina Lokacin da zan yi aure ya kusa in sha Allahu." Sadiq na dariya yace"Eh lalle to Ameen." Daganan suka cigaba da Tattaunawa kan lamarin na wani Lokaci kafin su yi sallama. A ran Sadiq yana jinjinama wannan yarinyar da ta iya sace zuciyar Tahir farat daya haka akanta ne kawai yaji Tahir ya nuna cewa lokacin da zai yi aure ya kusa. Tunda ya koma kullum da Safe in ya Kira Siya itama Sultana zai kirata yaji Lafiyanta. Ko da bazata amsa dakyau ba, shi dai daman Saboda ya Fita hakkinta ne. Ranar alhamis da ya kirata da daddare bayan sun gaisa ya ke kara mata Tunin inda Siya zata sauka. Kai Tsaye Sultana tace"Ni fa na gayamaka bani da masaukinta a gidana, kuma duka kayan da ke cikin gida nawa ne naga ba Dakin da bakomai a ciki ballatana kace na Sauketa aciki." Mamakinta ya kara kamashi Saboda Haushi sai kawai yace mata"Sulatana ki yi duk abunda ki ke so, lokacin ki ne." Daga haka ya katse wayarsa, Sai ya kira Big sis ya so ya fad'a mata abunda ya Faru tsakaninsa da Sultana ne sai kuma ya fasa a ransa yace ai shi Namiji ne shi zai Dauki matakin da ya Dace. Kawai sun yi mganar sai ranar lahadi zai zo gusau tunda sai Ranar asabar zai je zariya ya kwana washegari ya Dauko Siya su taho tare. Duk da Surayya sun yi waya da Hasiya ammh bata nuna ma Sadiq ba Tunda wannan kuma sirrin su ne ita da Matar kaninta kamar yadda shima kanin nata akwai sirri a tsakaninsu sun yi mganar Umma har ya gayamata abunda Umma tace masa Ranar da zai koma. Surayya ta yi dariya kafin tace"Ai Umma na kaunar yara nan ina jin nan gaba ana yayesu zata kwace muku su." Shima cikin dariyan yace"Sai mu bata, ina fatan mu samu wasu kafin a yaye sun." Surayya tace"Kai Sadiq, gwarne ka ke so Hasiyan ta rika yi? Yana yar dariya yace"Matar so fa ita ke gwarne kin manta ne Big sis.! Ta hararesa kamar yana ganinta kafin tace"Bansani ba sai ka fad'amin." Sai ya kwashe da Dariya ta na tayashi. Sun yi mgana Sosai akan Umma Surayya ta nuna mai su cigaba da addu'a in sha Allah Umma zata dawo yadda suke so. Daman har da zugan su Sajida kuma yanzu ta daina Biye musu. Sultana me suke samun nasaran yi mata Famfo son ransu. Shi fa Daman Sadiq ya sani Abubuwan da Sultana ta ke yi ba Wayonta ba ne. Shifa har mamakin Sajida ya ke yi, matar nan ko shed'an in ya ganta sai ya sara mata wajen Tsabar Munafunci. Duk zai kyalesu yanzu daman ya yi musu iyaka da matarsa su je ita kuma ta Biye musu su kaita su barota shi dai in ya gaji da tarata ya Faceta har Abada ta facu kenan bazai maida Dattin abunda ya fitar a hancinsa ba. kamar yadda yace Ranar asabar da misalin sha daya na Safe ya dira a Zariya ya iskeni na yi masa kyakyawan Tarba kamar yadda na Saba ni da ya'yana. ******** Daran yau dai su Asim ba su yi ma Babansu kara ba kwana suka yi kuka, bamu yi barci ba daga karshe ni yace naje na kwanta ganin akwai barci a idona. Yace naje na kwanta tunda ina jin barci shi zai kula da su, Allah Sarki bawan Allah duk farkawan da zan yi yana Rike da su duka yana Faman jijjiga in ya gaji ya koma ya zauna a gefen gado ya kwantar da su, ya Fara Daukansu d'aya bayan d'aya yana basu Madaran su. Ni uwace kukansu yasa na kasa natsuwa na yi barci dole na mike na isa garesa na mika Hannu ina Fadim"Assadiq kawo su, kaje ka kwanta ka yi tafiya akwai gajiya a jikin ka" Kallona ya yi cikin so da kauna kafin yace"ni nace kije ki kwanta Siya zan kula da su kinga ai sun fara rage kukan na su ko? Cikin wani yanayi nace"Haka muke fama da su, ammh na yau yafi na kullum wlh, kawo su kaje ka kwanta Tunda gobe muna da tafiya a gabanmu." Kin bani su yayi, yace sai dai na basu Nono na koma na kwanta. Haka na zauna yana rike da Asim na fara ba ma Asif Nono sannan na karbi Asim na bashi shima. Gaahi sun koshi sun kuma daina kuka ammh yaran nan sun ki yin barci idanuwansu kyar suna kallon kowa. Cikin Tausayinsa na kallesa Wlh akwai gajiya tare da shi, tare da barci ammh yaki zuwa ya kwanta. Cikin taushin murya nace"Kaga fa kana jin barci kawo su don Allah." Cikin Kaushinsa yace"Nace ki barsu ko? Ni da ba na zama ke fa kadai kike wahala da su yanzu na dawo ki bari nima na tayaki mana Siya." Yadda ya yi maganar ne yasa wani kaunarsa ya kara kamani naji wani Shauki na Dibana. Kawai sai na saka kaina saman kafad'arsa ina fad'in"Ina sonka Assadiq, na tabbata cikin maza Dubu sai an tona an kara Tonawa kafin a samu kamarka, Allah na gode maka Sannan yau na kara godema Amma da ta yi min kyakyawan zabi a Rayuwata.". Yana yar dariya yace"Ba kin ce baki so ba? Alokacin har rashin kunya kika so ki yi ma Amma wai baki sona? Dariya na saka ina fadin"Ba rashin so ba ne, kawai ina Duba manganun da ke kaina ne. Ina sonka Tun a Lokacin ka Fahimci mganata ba na son wani mummunan abu ya sameka ne ta Sanadina." Mirmishi ya yi mai Tsada kafin yace"ba abunda ya isa ya sameni face abunda Ubangiji ya kaddaromin acikin kaddarata." Kwanciyar da yaso na yi ban yi ba, hira na zauna muka yi ta yi, yaran nan kuma sai gabda asuba suka yi barci. Shiyasa sai bayan ya Dawo masallaci ne muka kad'aice da juna ta inda na kara sara ma magungunar gyara na marubuciya Surayya dee shine yadda Assadiq ya ke min rawan kafa da na Jiki in muka had'u da juna. Daganan na Bata Makin dari bisa dari kan duka mgangunanta na Sanyi da na gyara ga Gimbiyar kaza, tare da Tabntabaru Shiyasa ni yanzu ba na siyan kowani kayan gyara sai ta hannunta, kayanta masu inganci ne sosai +234 803 277 3332. Da safe kuma sai shirin Tafiya Daman na gama shirya akwatina da na yara. Tare da Tsaraban da zan tafi da shi da ko Assadiq bai sani ba. ya dai ganni da Ledoji har sai da ya yi mganar na Dauki a ledoji kamar wata bafullatana. Ina Dariya nace"Ita ce baka yi b'atan kai ba." Karfe goma saura muka bar gida na yi sallama da Maman suhailat da Ummi da ke gida daganan muka Biya gidan Adda Fati na karbi sako, ba ma mu shiga ba ita ce ta leko muka gaisa da ita har ta leko mota ta na yi ma su Asim wasa da suke kan jikina sai Faman ware ido suke yo suna gane gane. Watansu fa Biyu ne da wani abu ammh har sun yi wayau, ga shi sun yi Kiba gwanin ban sha'awa. Haka muka Dauki hanya muna tafe muna Hirarmu ta masoya gwanin ban sha'awa kuma kamar yara nan su san tafiya tsit sukayi daga karshe ma sai barci suka yi ta yi, sai gabda zamu isa sannan suka Farka. Muna hanya Ramatu ta kirani nace mata mun kusa isa ma, sai ta yi mana Fatan sauka lafiya. Kafin isarmu Umma ta kirani shima ta kirashi yafi sau uku tana tambayan muna ina? Muka ce muna hanya. Tace to mu fara sauka ta gida tukunnah. Alokacin har ya kalleni yana Fadin"Siya kinga abunda na ke fad'a miki ko? Watarana Umma zata kaunace fiye da tsamnanin ki." Sai na yi mirmishi kafin nace"Hakane,  daman ka sha fad'amin watarana komai zai zama Labari." Mun isa Gusau Biyu da wani abu na rana Tunda Assadiq bai yi gudu ba Sosai. Tarba da na samu a gidansu Assadiq ban taba Tunanin zan sameta ba, Umma da kanta ta fito ta tarbanmu, ta fara kwasan jikokinta bakinta har kunne, ni kuma Siyama da Farida na yi min barka da zuwa. Shashen Umma na fara sauka ni da kaya, ta kaini dakin da Sultana ta zauna tace na yi sallah kafin a kawo abinci. Su Asim kuma Tunda muka zo suka bar hannuna, suna hannun kakarsu sanda Su Siyama suka kawo min abinci naga asif a bayanta ta Goya tace min Asim na bayan Umma shima sai barci ya ke yi. A raina nace Lalle yan Biyu kyautar Allah, Assadiq kuma ashe gida ya tafi sai da muka yi waya ya ke gayamin. Har yana Tsokana da cewa"Gwara na bar ki da surukarki ku gaisa da kyau." Ina gama cin abinci na fito falo na kara gaida Umma ta amsa cikij yar sakewa, har tana ce min me na ke bama su Asim sun yi wayau da girma haka? Kaina na kasa nace mata madara ce kawai. Ita kuma kai Tsaye tace"Kina da nono mai kyau ne." Na dad'e zaune ita ta na Dauke da Asim sai faman jijjigaahi take yi da ya Fara kuka ni kuma ina zaune a kasa cikin Ladabi. Ganin ya ki daina kuka yasa ta Saukoshi ta bani shi tace na bashi Nono, kunya ta saka na kasa bata a gabanta da ta Fahimci haka sai ta Shige ciki ta barni sai da na gama bashi ta fito. Da kanta tace naje na gaida Mama da innani na kai musu yaran su gansu. Kila ma naga su siyama shaahen mama ko na Innani Asif na Hannunsu. Ban yi musu ba na mike, gani ta yi ina Kokarin ijiyesa saman kujera da Sauri tace"Ya zaki ijiyesa? Cikin Ladabi nace"Zan dauko wani abu ne Umma." Da sauri ta kariso ta karbesa ta na fad"in"Sai ki bani shi na rike miye amfani na? Ni dai ina jin kunya na mika mata shi, ta karbeshi ni kuma na shiga ciki na dauko Tsarabata na ciro na Umma da na Mama sai na Innani, sauran kuma na Abba ne da su Siyama har da Sultana ma na yi mata tsaraba. Ina fita falo da leda a hannuna na duka a gabam Umma na ijiye mata ina fadin"Umma tsaraba ce ba yawa." Sai naga ta washe baki kafin tace"Ah harda wahala? Masha Allah Allah yasa albaarka.* Bata Bude ba sai da ta bani Asim na rike a hannuna sannan ta zauna ta Bude ledan. Yaji ne da ya ji  dakada Nama da Tarfanuwa gashi yaji maggi. Sai Turaren Wuta na daki da Humra. Umma ta washe baki ta dago ta na kallona kafin tace"Wa ya gaya miki duk abunda na ke so haka?ko magajin gida ne? Mirmishi na yi mata batare da na yi mgana ba, Anty Surayya na kira na Tambayeta ta fadamim Umma na son Yaji sannan a bata Turaren kamshin Daki da Humra ta na Daraja wannan kyautar. Kuma naga haka, Domin ta nuna min jin Dadinta Sosai ta na min godiya karon Farko da ta kalleni tace"Nagode Hasiya Allah ya yi albarka." Na amsa da Ameen cikin jin dadi, Sai ta Bude yajin ta lasa ta fara Santi ta na kara min godiya. Shigowar Farida yasa Umma tace ta rike ledojin mu tafi bangaren mama. Farida na gaba ina baya rike da Asim zuwa bangaren Mama. Na iske Anty Sakeena a bangaren Siyama ma ta na ciki Asif na Hannun Mama itama ta reno. Tana ganina ta washe baki ta na fadin"Kaga fara mai Farar Aniya, ana zencen ki sai kuma a ganki." Mirmishi kawai na yi, Sakeena ta tashi ta karbi Asim a hannuna.. Ni kuma sai na Duka kasa ina gaisheta ta amsa cikin kulawa. Na juya na gaida Anty Sakeena itama ta amsa cikin Fara'a kafin tace"Yara nan fa girmansu ya bani mamaki kamar sun yi wata Hudu' wai sannu da kokari." Mirmishi na yi ban yi mgana ba, na karbi leda guda daya hannun Farida na tura gaban Mama ta dauka ta na fad'in"Me kuma muka samu? Sai taga Turaren rushi sai na Tsinke masu kamshi Tafiyayye d'an maiduguri wajen makociyar Adda Rukkaya na siye shi." Mama ma nata godiya har Anty Sakeena sai da ta yabi Turaren nan tace Umma zata san mata. Siyama na kallah ita da Farida kafin nace"Kuma tsaraban ku na nan sai kun zo amsa." Sai suka fara Murna, na jima a bangaren Mama sannan Sakeena ta Rakani har Bangaren Innani. Mun isketa kwance baiwar Allah ashe bata jin dadi zazzabi ta kwana dashi ta kuma hana Farida ta fad'a ma kowa . Shuru shurun da ta yi mana ne yasa muka san bata da lafiya. Sakeena ta aika Farida ta kira Umma tazo ta gani. Sadiq ta kira ba jimawa sai gashi yazo Tunda Abba baya gida. Innani bata son asibiti dakyar ta yarda Sadiq ya bata abinci a baki ya kuma bata maganin ciwon kai. Yana ta ma Faridan fad'an ta daina Biye Innani da ta ga wani matsala tazo ta yi mgana. Yarinyar ta bani Tausayi sai sharan kwallah ta ke yi, a bagaranta muka zauna da Sakeena ashe ta na da mgana muna ta Hira da ita. Mune har mangariba,Allah Sarki Innani sai gashi taji Sauki har ta na Daukan su Asim. Ita Nama na kawo mata soyayye Saboda Anty Surayya tace ta na so, aiko na sha addu'a da Godiya. Anty Sakeena ta tafi gidanta ni kuma ina Tare da Innani a bangarenta tare da su Siyama. Bayan isha'i sai ga Assadiq da Abba sun shigo Dubata anan muka had'u da Abba na duka ina gaishesa. Assadiq kuma ya kwashi su Asim ya kai masa ya rikesu yana Dariya. Mun gaisa dashi Cikin sakewa kamar yadda muka Saba. Ya saki jiki muna ta Hita daga karshe har Umma da Mama nan shashen  suka dawo suma. Anan kuma suka ci abincin dare ni dai Saboda kunya ina cikin Dakin Innani ni da Farida. A falo kuma Abba na ta yi ma su Umma Tsiyan sun ga fararen maza sun yi masa kishiya. Mama taja Asif tace shine mijin Robanta Umma kuma ta rike Asim. Innani na zaune tana dariya a ranta tana jin wani Farimciki ganin Sulaimanu cikin Annushuwa. Sadiq ma ransa Fes sai mirmishi ya ke yi. A daran Surayya ta zo min Sannu da zuwa, Abba ne ya yi ta fad'an me yasa ta fito bata bari sai da Safe ba. Shiyasa bata dade ba ta tafi gida, ni kuma Assadiq yace na shirya mu karisa can gidan, Kafin mu tafi na bama su Siyama Tsarabansu na mayafai sai kayan kwalliya. Abba kuma Turare mai kamshi na kawo masa ya yi ta saka min albarka. Su Umma sukaji kamar kada su barni na tafi da su Asim suna ta cewa Gobe da Safe suna jiran magidanta nasu. Sai goma na Dare muka isa gidan Assadiq. Gidan ya yi min kyau, madaidaici da Shi da zamu shiga megadi na gaisheshi ya amsa yana gayamasa ni ce uwargidansa ga ya'yansa nan. Megadin bahaushe ne ya yi ta saka ma su Asim albarka. Bansan cewa Sultana bata so saukata a gidanta ba sai da muka iso muka iske ta Rufe kofar falo. Sai dai ta manta yana da key din gidan tare da keys din motarsa ya ke a had'e da shi ya yi amfani ya Bud'e mana muka shiga. Yadda na gane matar gidan bata maraba dani, shine har wutan dakunan takashe ko'ina Duhu sai da ya kunna Haske ya gauraye. Nice na ke ta bin ko'ina da kallo shi kam yana rike da Asif shi ya shigar min da akwatinana dakin da ke yamma da falon. Shima a kulle ne sai da ya saka makulli ya Bud'e. Bakomai a dakin sai gado sai wardrope akwai kuma Tiolet aciki sai Cafet sai dai gadon karami ne ba babba ba. Kamar yadda na lura gidan Bedroom guda uku ne, biyu suna waje daya Daga yana bangarensa na Dabam. Yadda bai ce min komai ba nima ban ce masa komai kan Sultanar ba. Shi ya taimakamin na yi musu shirin kwanciya. Da yake da yamma Mama ta sake yi musu wamka tun a gidan ma suka Fara barci, nima sai yace na yi shirin kwanciya ya duka ya sumbaci kuncin su Asim sannan nima ya duka ya Sumbace. Lokaci daya yana fadin"Sai da Safe Matar Assadiq.' Nima ina mirmishi nace"Sai da Safe Mijinsiya." Yana mirmishi yace na Rufe kofa kuma sannan na yi addu'a kafin Fitarsa har A.c da fanka sai da ya Tabhatar da ya kashe min. Ni kuma sai na Shiga Tiolet na kama Ruwa na zo na yi shirin kwanciya bayan na yi addu'a na Tofe jikina da na ya'yana na Rumgumesu bayan na Rufe kofar da key ta ciki..ban ksshe wuta ba Saboda su Asim na motsawa suka ga Duhu za su fara rigima. Barci na sha sosai sai Asuba na Farko ko da Assadiq yazo yana bugamin kofa a lokacin ina sallah ne. Bayan na idar na tashi naje na Bude kofar na dawo, yaran nan sun yi barcin Dare ammh da Asuba nan suka fara kuka duk suka rikani. Asssadiq kuma bai Dawo daga masallaci ba, kukansu har haraban gidan nan Ammh Sultana bata Fito ba. Shine ya dawo masallaci yaji kukansu ya Shigo da gudu dakin yana Tambayar Ba'asi. Cikin gajiya nace"Bansani ba, kawai a tare suka farka suka fara kuka." Allah Sarki Assadiq haka ya Rikenin Asim da Asif a tare yace na had'a musu madaransu. Ba ruwan zafi shi ya ce na fito muje kitchen ya nuna min komai yace na Dafa Ruwan zafi. Haka ko akayi ya jirani na Dafa ruwan Dumi na Dama musu kowannen na cika masa Fidansa, falo muka Fito ni da shi Saboda yadda suka Rikitamu da kukansu shi yana ba wa Asim ni kuma ina rike da Asif ina bashi. Bamu san Fitowarta ba sai ganinta muka yi a saman kan mu. Kere kere tana kallon mu, ko Darajan yana mijinta bata gaishe shi ba sai nice na gaisheta ta yi kamar bata ji ba ta wuce ta shiga kitchen ta na sakin karamin Tsaki. Kallona ya yi rai bace kafin yace"Kada ki kara zubar da  girman ki, ki gaisheta in bazata gaisheki ba ta bar shi." Cikin nuna komai ba komai ba nace"Haba bakomai ai ni nazo gidanta." Bai kara mgana ba ammh Daga gani ranta ya baci, muna zaune ta fito ta koma dakinta d'auke da Mug a Hannunta. Allah ya taimakemu suna sha suka daina kuka daman rigima ce da Yunwa kuma. Ban dauka Haka Sultana ta yi nisa da Tsanata ba sai Ranar, ko Abun kari bata yi mana ba ballatana Ruwan zafin da zan yi ma yara wanka Tunda Tanki ya lalace ruwa baya zuwa ta makewayi. Bansani ba ko yaje ya yi mata mgana ne, naji tashin muryansa ya na yi mata mgana ammh ni ban ji nata muryan ba. Sai da ya shigo ne na gansa ransa a b'ace yace ko zan shirya ya kaini gida ne can sai na karya nayi wanka suma yaran su yi? Ni kuma sai nace haba ni zan iya yin komai indai yabani izini. Shi ya rikemin yaran na shiga kitchen na Dafamana Ruwan Tea da Soyayyen kwai da Buredi da shi muka karya sannan na saka Ruwan zafi na yi ma yaran wanka yana tayani. Bayan na shiryasu ya rikeminsu nima na yi wankan na shirya shima kuma sai yaje ya yi wankan ya shirya cikin manyan kaya tunda yanzu naga ya rage saka kananun kaya. Har muka bar gidan nan Sultana bata fito ba, yana ijiye ni bai ko shiga gidan ba ya juya yace akwai inda zai je. Naga ransa a bace ya ke na yi kokarin jansa da Hira ammh bai saki Jikinsa ba. Ni dai bakina kanin kafata ban gayama kowa abunda ya faru acan ba,  bangaren Umma na sake sauka sai dai naje na gaida mama da Innani da ta yi ras da ita na dad'e a wajenta muna ta Hira Sai Abba shima da na jima a bangarensa muna gaisawa. Sai can da rana sai ga Assadiq da Anty Surayya ta kawomin sinasir da miyar Naman rago. Shi a lokacin yace zai kama hanyar Abuja ya kirani har mota ya ce min kada na rika biyema Sultana Don Allah kuma tunda baya nan na rika Tafiya da Siyama in gari ya waye sai mu dawo gidan su Umma. Ni kuma sai naga ai wahalace cikin Sanyin murya nace"Ni dai ka barni wajen Umma Assadiq don Allah." Cikin Fushi yace"To ni sa'anta ne da zan ce ga abunda za'ayi tace a'a." Ni kuma ganin ya harzuka sai na Shiga lallashinsa ina nuna masa bakomai ya barni na zauna a wajen Umma sai yace min itama Surayya haka tace. Dakyar ya amince na zauna wajen Umma, sannan anjuma na aika Farida da Siyama su daukomin kaya nace to. Ko da Umma taji nan wajenta zan karishe kwanaki bata damu da Tambayar ba'si ba a tunaninta ko kila Saboda tafiyar Sadiq ne. Ni kuma sai hakan yafi min kwanciyar Hankali Tunda ni bani son abun Rigima ko kankani. Sai na koma kwana bangaren Umma komai yi min ake yi, hatta wankan su Asim kayansu sai dai a kawomin su an wanke su tas. Ni ce ma ke yi ma Umma shara da wanke wanke da gyaran dakinta. Shima tayi ta cewa na bari nice ban saba zama ba. Sai gashi Umma har sai ta tambayeni me zan ci? Nace duk abunda aka bani zan ci. Yara kuwa sai in suna kuka a kawoni na basu nono, madaran su kuma su Siyama sun iya had'awa bani da matsala. Anty Surayya ta rakani da Umarnin Umma naje gidajen yan'uwan Assadiq, gidan Anty sa'ima da Sakeena sai gidan Anty Sadiya da Anty Sa'adatu har gidan Sajida mun je. Ita dai sai wani yamutsan fuska take yi shiyasa bamu dad'e ba. Washegari kuma ta zo gidan ta yini a bangaren Umma tana ganin komai. Tana tashi daganan ta Biya wajen Sultana tace mata sai ta zauna bata Haihu ba  ga Umma can ya'ya yasa Hankalinta ya koma kaina ta fara ji dani kamar kwai a miya. Aiko itama Sultana sai gata tazo gidan Ahalin tunda muka zo bata zo ba har sai da Umma ta mata tsiyan idonta kenan? Sai tace wai bata jin dad'i ne. Taganin ma Idonta ganin Umma ta goye Asim ta na ta kuma lallashin Asif da ke hannunta. Gidanta ta yini kuma bata min mgana ba nice ma na gaisheta ta amsa kamar bata so. Yara kuma ba ta taba Daukan su ba. Tsaraban da na zo mata da shi na Humra na Dauko a gaban Umma na bata ta amsa a wulakance Da farko ma kin amsa tayi sai da Umma tace"Karb'i mana Sultana." Shiyasa ta karba ko ta gode batace min ba, nima ban nema ba tunda domin Allah na yi. An kira sallar la'asar Daga ni har Umma muna salla, ni ina cikin Daki Umma kuma a falo take sallarta su Asim sun yi barci ta kwantar da su. Shine suka fara d'aya na fara kuka d'aya ya saka kuka. Suka fara yi kamar jiniya  Sultana na gefe kafarta daya kan daya ko ta daga kai balle ta Kallesu. Cikin Tausayi Asim saboda kuka ya fad'o daga kan kujeran. Umma na salla tunda suka fara kuka take Ihin ihim ammh ko ajikin Sultana. Ni kuma na sallame ammh kunya ta hanani fitowa. Inajin sanda wani cikin su ya fad'o ya Tsandara Ihun da kowa a gidan sai da yaji. Umma bata idar da salla ba ta yanke ta Dauki Asim da Sauri ta na jijjigashi sai ga Mama itama da Gudu tana tambayan taji kukan su Asim lafiya? Umma na kallin sultana cikin bacin rai tace"Ina salla ne, uwar ma ina jin sallar take yi. Sultana na zaune inda take nan ammh yarinyar ko a jikinta ballatana tasan suna yi har Asim ya fad'o daga saman kujera bata daga daga inda take ba sai ni ce na katse sallar na Daukesa." Mama na kallon Sultana lokaci daya ita ta Dauki Asif ta na fadin"Ke kam sultana baki kyauta ba, ina Ruwan kishi da yaro kuma?. Umma tace"Sakarci mana, yara ne fa kuma kada ki duba komai ki Duba suma ai ya'yanki ne." Kai Tsaye Sultana ta mike tace"Ni ba ya'ya ba ne. A bari in na haifi nawa sai ace musu ya'yana." Mama ta kama baki Umma kuma da ranta ya baci, Ga Asim yaki barin kuka yadda take jin yaranan har ranta. Cikin Tsawa tace"To mun ji mara kunya, sai kije ki haifi naki shashasha kawai." Kawai sai Sultana ta saka kuka ta Dauki mayafinta da Jakarta ta Fice da gudu tana kuka . Mama ta koma ta zauna Rike da Asif tana fadin"Kai sultana taki yin hankali." Umma tace"Kar ma ta yi, ai na daina saka baki a kanta in Sadiq din ya gaji ya saketa tunda bata san mutumci ba, yarinyar nan nasan iskancinta ya hana Maman yara nan zama gidan mijinta yace ta dawo wajena  ko da bai gayamin ba na Fahimci haka kuma da sanin Halin sultanan." Mama tace"uhm ai nima na saki da Lamarin Ubangiji Umma, ki duba da ashe rabon yaran nan ne komai ya faru, ni kwanakin nan Naji labarin Yaron nan abokin wasan mu da kwanaki na taba fad'a miki an ce bazai auri yarinyar da ya ke so ba? Umma ta gyad'a kai Mama ta cigaba da fadin"To wlh ya auri zabin uwar tasa, ammh fa ya ribace yarinyar nan sun lalace a waje karshenta dai an haifa mata Shege a waje." Umma ta zaro ido kafin tace"Innalillahi wa'inna ilaihirraju'un. Kai Allah ka rabamu da mummunan kaddara, to ina dad'in shi don Allah." Mama tace"Ina fa dadi ai Sadiq ya yi Tunani sosai." Umma ta yi shuru jikinta ya karayin sanyi. Mama kuma ta cigaba da bata Labarin dalilin haka uwar ta fadi ta samu Mutuwar barin jiki. Umma sai salati take yi, ta na kallonsu a Asim. A fili ta furta"Sai yanzu naga Ribar auran Yarinyar nan, sai kuma yanzu na yadda da mgamar Abban siyama da yace tunda akwai Rabo a Tsakaninsu in da ba su aure ba to fa ta hanyar  banza za su samu duk Rabon da Allah ya Tsaga a Tsakaninsu." Mama tace"Shiyasa na saki komai,suma yaran nace wlh su bar adawa da Hukuncin Allah." Kukan su Asim ne ya hansu hiran dole Mama ta kwalamin kira na fito sai Umma ta kalleni ta na fad'in"Kina jin yara na kuka kin ki fitowa Hasiya? Cikin jin kunya nace"Ban ji ba ne Umma." Mama tace"Zo ki basu su sha, balle Asim da ya sha kasa." Kasa ba su nono na yi a gabansu sai na Rika karbansu d'aya bayan d'aya ina Shiga da su ciki. Mama ta kalli Umma tana fadin"Wlh tana da kunya, ta fa ji kukansu kawaici ne kawai." Jinjina kai kawai Umma tayi, itama taga kunya a tare dani sai dai ta wannan tabon da ke gareni ne ke damunta duk da ta fara Fahimtar Allah ne fa sarkin kowa. Washegari Lahadi tun safe muka yi shirin tafiya Umma taso mu kara kwanaki Assadiq da suka yi mgama ta waya yace zan fara Tp shine Dalili sannan Saboda Haihuwa har aka tafi Hutu ban fara zuwa ba. Ni kaina naji kewarasu bako Rab'a akace, Umma ta siyama su Asim kaya Mama kuma ta siya musu kayan wasa ni kuma Umma ta bani leshi mai Tsada da Takalmi sai wata Atamfa da tace na kai ma Mahaifiyata. Abba kuma ya bani kudi, Innani ma ba'a barta a baya ta bama su Asim 500. Anty Surayya kuma ta bani kyautar Mayafi da takalmi masu kyau da tsarin sun yi min sha tara na arziki. Direban Abba ya kaini har gida abun sai Godiya na kira Assadiq ina gayamasa abunda aka yi min a Gusau. Shima cikin jin dadi yace"Kema ai kin yi musu abun alheri baki gayamin ba, sai da Umma ta gayamin to kada ki damu domin sun rama ma kura Aniyarta." Sai kawai nayi Dariya, Nayi Farinciki sosai kuma shima ya Fahimci haka. Tun a ramar muka yi waya da su Umma nace mun sauka lafiya. Tace a gaida mata mazajen su ita da mama. Ina dawowa na kira Habiba tazo Saboda ta tayani gyaran daki da kula da yara. Na kira su Adda ina ba su Labarin naji dadin zuwana gusau da abun alherin da suka yi min. Amma ma na kirata nace an yi mata kyautan zani ta na ta godiya. Da Safiyar Litini tare muka fita da Habiba, ta wuce makaranta ni kuma ma tafi inda na ke Tp. Na basu uzurin ba na nan sukace bakomai sun bani aji Hudu, sannan akwai Nanny mai kula da yara ita sukace na rika bar mata su Asim kafin a fita break, in anje Break sai nazo na gansu na basu nono. Sai abun yazo min da Sauki ganin na jima ban fara ba, sai na saka Pressure ballatama da akace Supervisor d'in mu suna kan hanya Tunda bai wuce wata daya da wani abu mu gama Tp din ba. Ina jin dad'in malaman makarantan Sosai harda mai makaranta ga sauki kusa da gida bani da wata matsala. *Janafty* *TMWB3K015* *TMW is a paid Novel, Pay 500 for regular or VIP N1K, Via 0552179550 Jamila Umar Gt bank, 09069067488* https://chat.whatsapp.com/K3rO5UonX4GDVxtQbA5mZl PAID ADVERT✅ Assalamualaikum wa rahmatullahi ta'ala wa barakatuhu!!! Wannan group din dai na komai da komai ne. A taiqaice *Farashin mu na daban ne compared to sauran Yan kasuwa *Kaya masu kyau da quality. Abinda kika zaba shi za a Baki * Swift delivery.watau waybill a sauqaqe da Yardar Allah * Muna sake New Arrivals ka fin su cika Gari * Muna iya duba maku kaya a good price ko da ba namu ba ne idan kuka Aiko da hoton kayan Allah sa mu qaru da juna Ameen *BAYAN WATTANNI BIYU.* Wattanin Biyun da suka gabata duk ba su zo ma Sultana cikin Dad'i ba. Domin ta yi su ne cikin Kunci Tsananin kishin Hasiya da ke cinta a ranta ya haifar mata da Zarge zarge na banza da wofi. Bata da aiki sai kunci da kuka, ita gani ta ke yi duk abunda ake yi mata ba aldaci ake yi mata ba Yaya Sadiq yafi son Hasiya a kanta sannan Umma ta fara karka akanta daga karshe ma har Gorin Haihuwa ta yi mata Saboda Kaunar da ta ke yi ma Ya'yan Hasiya. Kuma saboda wauta irin nata ta samu duk ya'yan Umma da ke zugata ta fad'a musu Umma ta daina sonta har Gorin ma Haihuwa ta yi mata. Magana kuma taje kunnen Umma daya sa Ranta ya baci tace a gayama Sultanan ta yi mata gorin Haihuwa in taji hauahin Gori gobe ta ganta da Ciki. Shikenan Sultana ta kwazzabi kanta ita sai ta yi ciki saboda ta Haihu, ita ma Umma ta fara kaunar ya'yan da zata Haifa ta daina kaunar su Asim da ta Tsane su su da uwarsu gabadaya. Kuma in dai ta Fahimci baka Goyon bayanta a zagi Hasiya ko kuma taga kana bayan Sadiq sai ta janye jikinta dakai. Yanzu Sadiya ne da Sajida abokan shawaranta sai Salima da ita ce ke kiranta ta na kara nuna mata bakin Hasiya a wajenta, tunda Salima ina ne bata taka a dangin su Hasiya ba? Labarai sai wanda tace bata so, haka ya'yan su Baba tanko da su Baba Saminu ke bata wasu labaran in sukaje Zariya wasu ma Labaran duk na karya ne. Su ukun nan da kamashon su wajen kara tabarbarewan zaman aure Tsakanin Sultana da Sadiq, tunda shi ya kasa gane mata tun bayan bayyanar Sirrin da ya Boye na auransa da Hasiya. Duk sanda zai zo mata weekeed ba sa Rabuwar dad'i duk iya kokarin da ya ke yi sai Sultana tace ita yana Danne mata hakki sannan ya fi son Hasiya akanta har tunanin cewa ita fa a budurwa ya aureta ya kamata ya fi sonta ba ya rika nuna ya fi son Hasiya da ya aureta a bazawara ba. Kuma duk Sajida ce ta saka mata wannan Tunanin na cewa hasken Fata kawai Hasiya zata nuna mata ammh jikin mata ta fita komai da ilimi da komai ita Hasiya Jahilar banza ce. Sai daga baya take jin Hasiya da iliminta Tunda har Karatun Nce take yi a yanzu shima sai da ta tada masa Rigiman itama makaranta zata koma. Shi ko yaso ya tafi da ita Abuja Tunda mganar Loan din gidan da za'a basu ya tabbata. Tunaninsa sai taje can ta cigaba da karatunta ita kuma Hasiya sai ya dawo da ita nan Gusau, ammh Zargi da kishi suka rufe ma Sultana ido ta kafa masa kahon zugan Tunda Hasiya na karatu itama karatu zata koma shi kuma ba tashin hankali yace Allah ya bada sa'a, in an fara saida Jamb ta yi masa mgana ya siya mata sai ta Rubuta shi ba shi da matsala. Duk irin abubuwan da ta ke yi masa bai taba daga baki ya kai karanta gaban Umma ba, gwara ma wani Lokacin ya na yin mganar da Big Sis, ita kuma sai ta rika Tausan shi da yarinta ke damun Sultana ya yi mata Uzuri, shi kuma abubuwa da dama ya ke dubawa ciki harda in yace zai Dauki mataki a kanta Umma ya ke ji, sannan mutane za su ce saboda Siya ne ya yi haka kenan zai goga ma Siya abunda bata san faruwarsa ba. Ita kuma Surayya ta san harda Zuga ke dawainiya da Sultana kuma tasan masu zugata bata so ta gayama Sadiq ne tunda akwai yar matsa tsakaninsa da su Sajida har gobe bayan gaisuwa wata hira da ke shiga tsakaninsu a baya yanzu ta kare..shi ya riga ya tsame su gefe suma kuma suna ganin suna gaba da shi, shi ya kamata ya bi su. shi kuma ta bakin shi yace ba su Haifeshi ba sannan su suka Tsallake Hurumin da ba na su ba. Kuma su dai suna iya bakin kokarin su wajen gayamata gaskiyan ta kwantar da Hankalinta ta zauna lafiya da mijinta watarana sai labari, ammh sai take ganin kamar ba gaskiya suke fad'a mata ba. Ba gidajen su har wajen Umma ta Dauke kafa ta Daina zuwa  ita kuma Umma ta yi fushi tace a kyaleta Tunda Sultana ta nuna ta na da wacce ta fita, ta koma ta kama yan'uwanta na Shinkafi tare da matannin Ubanta shikenan. Ita Umma Taurin zuciyar Sultana da Sakarcinta yasa ta fita sha'aninta, da abunda ta ke nunawa na Tsanar ya'yan Sadiq kiri kiri a gaban mutane ita bata damu in ta tsani Hasiya wannan Dabam, ammh yaran fa? Ko ta manta ba jinin Hasiya ne kad'ai ne a jikin yaran ba har da jinin Sadiq, kuma in da alkwari ai Ruwa bazai yi gangancin Dafa kifi Sadiq dan'uwanta da duk inda taga jininsa abun karramawarta ne, ballatana yanzu da ya ke matsayin mijinta. Tasan da Farko har da ita wajen saka ma Sultana Tunanin Banza ammh Daga baya ta maidata gidan mijinta ta bata Shawaran ta zauna ta yi masa Biyayya da kissan nan na mata ammh Sultana bata ji mganarta ba, ita kuma yanzu Tsakani ga Allah yadda ta ke son yara nan duk wanda yace baya  son su itama bata kaunarsa. Sannan Tunda Mallam yace in da ace Sadiq bai auri Hasiya wannan Rabon ya'yan da ke Tsakaninsu ko da aure ko ba aure sai sun zo duniya. Acikin zuciyarta taji ta saki komai, ta kuma san inda a lokacin Sadiq yazo da mganaar auran nan tana cikin yan gaba gaban hana lamarin, da Faruwar haka kuma daga baya azo a haifi d'a mara ido ai sai tace gwara da ya yi auran Boye duk daga baya gashi an samu mafita. Kuma ta fara saki da kiyayyar Hasiya tunda bata taba kamata da wani hali na banza ba, balle ma zuwanta taga kunyarta da Hankalinta da Biyayyarta illarta Daya wannan bakin Canfin da ke tare da ita shi ke kara sanyayamata da Gwiwa, bata kaunar wani abu ya samu magajin gida da gaske ne d'aya Tamkar da Dubu ne. Ita ce silar had'a auran Sadiq da Sultana tafi kowa son ganinsu tare, kuma ta na son ganin jikokinta ta Tsatson su, Sultana ita ta Rikete tun tana karama Sadiq kuma ita ta Haifeshi tana son su matuka, Soyayyar da ta ke yi musu ne ma yasa ta so kasancewarsu matsayin ma'aurata sannan zata fi kowa Murna in Sultana ta Haifa mata Jikoki. Sai dai Rashin kunyar da Sultana ta yi mata sannan ta Dauke kafa da wajemta bayan taje ta na yawo da ita wai ta yi mata Gorin Haihuwa yasa Umma ta fita Batunta bata kuma kara bi ta kanta ba. Kuma hakan da Sultana ta aikata ba wai wani jin dadi ya kara mata ba, kullum tana cikin kunci duk ta rame ta lalace sai kace ta na cikin Wahala. Abun takaici shine kishin da Zargi sun kasa barinta ta samu sukunun zuciya. Sadiq har fargaban zuwa Gusau ya ke yi yafi Murna da jin Dadi in yaje Zariyq Saboda yasan har ya gama kwanakinsa ya koma Faranta masa kawai siya zata yi, duk hanyar da zai Shiga Damuwa ta na nisanta kanta da shi. Ita kuwa Sultana hanyar da zata bata masa ta ke nema, kuma komai zai yi mata sai tace bai yi mata adalci ba ga Zargin bala'i, satin karshe da ya sauka a Gusaubsai da ya yi mata kaca kaca haka suka Rabu zukata ba dad'i. Bai san waya zaunar da ita ya karanta mata Ranar jumma'a ya ke zuwa zariya ba sannan kuma wai baya tafiya sai Ranar litini. Kuma ita sai yazo mata Ranar asabar ya yi kwana daya ya koma ranar Lahadi, har ds cewa ita bata yarda ba in ma ana zaluntarta ne bata yafe ba. Ya dad'e yana kallonta bakinsa a bude yana Tunanin wani irin sake ne ya yi ma sultana haka da ta rainasa? Tsabar ransa ya baci ko bayani bai tsaya yi mata ba ya balbaleta da Masifa daga karshe yace an zalunceta ta jima bata yi Allah ya isar ba. Ita bata ga yafi zuwa wajenta sosai saboda su Umma ba, Siya sai ya yi sati biyu har uku bai je ganinta ba. Da Sun yi waya ya bata hakuri zata ce bakomai ita Kwanciyar hankalinta tajisa Cikin koshin lafiya. Gusau kuma ya rantse da Allah in ya Dad'e ne ya yi sati Biyu bai zo ba ammh duk da haka bata gani ba har tana kiransa da azzalumi. Ya fahimci wani abu ta na Dauka wani Rayuwa Siya ta ke yi mai kyau din da ta fi wanda take ciki, ita bata godema Ni'imar Allah da ta ke cikin Gidansa Ba na Haya ba, Allah ya jikan Siya da gidan Haya ta ke zaune kuma bata taba yi masa korafi ba ta zauma da shi Tun bata san cewa shi wani ne ba. Shiyasa har Gobe Siya ta kwashe matsayi mai girma acikin Zuciyarsa, ita kuma Sultana abunda ta ke yi bata san a sannu sannu take sire masa ba. Shiyasa wannan karon ya yi tafiyarsa Zariya wajen Siya da su Asim da suka kara wayau suna da wajen wata Hudu da kwanaki, kuma Satin Gusau ya kamata ya je da kuma ya koma Abuja. Ya share kafa ya yi zamansa sai dai ya kira su Umma a waya. Da an tambayesa shuru bai zo ba sai yace aiki suka yi masa yawa. Sai da ya yi wajen sati hud'u bai zo gusau ba kanwar naki sultana ta kama kiransa yaki ko amsa kiranta. Har Tasasai take turamasa na mangaganu ya yi kamar bai gani ba. Da kuma ya tashi zuwa ranar asabar ya shiga garin  kuma da yammah Saboda ya kara nuna ma Sultana kuskurenta Gida ya sauka sai can dare ya isa gidansa. Taji dawowarsa kila ko Siyama ta fad'amata ta yi masa abinci an ci gayu ammh ko kallo bata ishesa ba ta Riga ta ba'ta garinta a wajensa. Shi ya kona ma sultana rai ganin ta yi wahala ta masa tarba duk wulakantata da ya dinga yi ammh shine zai dawo tana yi masa sannu da suwa ya kalleta kamar yaga kashi ya shige ciki. Da wannan Haushin ta bisa ciki Fuu lokacin data shiga ta gansa yana Cire rigane a kansa ta tsaya Hannu rike da kugu ta na fadin"baka lura dani ba ne Yaya Sadiq? Ko kallonta bai yi ba sai ma kwanciya da ta ga ya yi  ya Dauko wayarsa ya na Dannawa. Kuka ya taso mata ammh sai ta Danne ta taka ta isa gabansa ta saka Hannu ta warce wayar. Kallonta ma bai yi ba sai kawai ya Juya zai kwanta nan take ta saka hannu ta Juyoshi ta na fadin"Kana ji ina mgana fa? Cikin kaushin murya yace"Me kika ce? Ya fad'a ya na kallonta Ido Cikin ido, Sai ta kasa mgana cikin wani irin zafin kishi tace"Na yi maka abinnci ka taso kaci." Kai Tsaye yace"Na koshi aci lafiya." Daga haka ya juya mata baya lokaci d'aya yana fadin"Ki tabbatar da kin ijiyemin waya kafin ki fita." Kawai sai yaji Sultana ta fashe da kuka da karfi harda jiniya. Ammh bai sa ya waigeta ba Cikin kukan ne yaji ta na fadin"Shikenan tunda ni baka sona ka sakeni na tafi Gidanmu mana." Yana jinta sai ya yi kamar bai ji ba sai  da ta kara maimaitawa sannan ya Juyo yana fad'in"Wani gidan kenan? Cikin gunjin kuka tace"In da ka auro ni, in kai baka sona Umma na sona." Wata bazawar dariya ya yi lokaci d'aya yana mikewa zaume kafin yace"Umma? Ke yanzu domin baki da kunya sai ki koma wajen Umma da matsalarki? Kin manta kin gama yawo da ita da cewa ta miki gorin haihuwa? Sai a lokacin Sultana ta dawo Hayyacinta sai ta dakata da kukanta ta na shan Shessheka. Cikin takaicimta ya kalleta kafin yace"Yau Umma na gayamin Abunda kika yi mata  ta na sharan hawaye, tace bata taba tunanin haka daga gareki ba Sultana, kuma don ma ban zaunar da ita na Fad'a mata irin abubuwan da kike yi min ba, Ai in dai kikace na sake ki ba gidanmu zaki koma ba tunda kince Umma bata son ki yanzu ko ki koma inda ake zugaki ana nuna miki abunda kike yi mai kyau ne, ko kuma ki koma Shinkafi tunda daman kince duk wanda ya bar gida gida ya barsa." Daga haka ya koma ya yi kwanciyarsa ya kara juya mata baya yana jan karamin tsaki. Shi kanshi ya sha mamakin Abunda Umma ta fad'a masa, bai dauka Jakancin Sultana ya yi tsanani haka ba. Sultana kuma sai a yau taji kunyar Nadaman mganganunta ga Umma, su suka taru suka Rufeta ta kara fashewa da kuka tana yi ta na yi har tana dire kafafu yana jinta bai kara bi ta kanta ba. Sai da yaji tana fad'ar manganuganunta cikin kuka ta ke fad'in"Ka yi wajen wata baka zo wajena ba, ammh nasan kaje wajen matarka kuma ka yi mata abunda ta ke so, ammh shine ni ka zo ka faramin wulakanci da nuna bani da Muhimmamci a wajen ka." Ta karishe fad'a cikin gunjin kuka yana kwancen yace"Eh baki yi karya ba naje wajenta, kuma ina yi mata abunda ta ke so kuma zan Cigaba da yi mata abunda ta ke so, tunda nima Abunda tasan ina so ko da ban Furta ba shi ta ke kokarin yi min, ki yi koyi da ita domin Siya ta na da Dukkan Sufofin Mace tagari." Ai Sultana najin haka kamar an Tsunguli bakinta ta bude baki tace"Shiyasa ita ka yi mata ciki ta Haihu, ni kuma da baka kaunata ka kasa yi min cikin da nima zan haihu." Sai kuka wiwi wiwi kamar wata karamar yarinya. Kamar wani gaula haka ya mike zaune yana kallon sultana. Cikin mamaki yace"Shima cikin kina Zargin da gangan na ki yi miki shi? Kai tsaye tace"Eh mana, ai ita da ka ke so yan Biyu ka bata, ni da baka kauna ko dayan baka bani ba wama ya sani ko yanzu wani cikin gareta." Cikin Mirmishin takaici yace"Ina fatan Allah ya amsa bakin ki sultana." Daga haka ya juya zai kwanta kawai yaji ta fado masa a jiki tana fad'in"Nima wlh sai ka yi min ciki, kuma nima yan Biyu na ke so." Kallonta ya ke yi kamar yaga Mahaukaciya sabon kamu. Cikin kaushin Murya yace"Ke dagani ba na son sakarci." Sai kawai ta kara sakamasa kuka tana fadin"Nima ai ina da hakki a kanka in bazaka bani ba shima sai ka fad'amin." Shifa ya fara Tunanin ko Sultana kwakwalwarta ba lafiya, bai isa ya ce bazai yi mata abunda ta ke so ba Tunda itama ta na da Hakki a kansa. Duk da ransa baya so hakanan ya Danne zuciyarsa ya biye mata ya bata Hakkinta kamar yadda ta ce. Yana samun natsuwa ya tashi ya barta nan kwance yaje ya Tsarkake jikinta ita Tsabar ma sakarci da kishinta na Jahilci bai sa ta Fahimci mace na son gyara wajen dawo da Hankali miji a kanta ba. Tana kwance cikin bargo ta na kallonsa yana Tsane ruwan da ke kansa daga murya ta yi tana fad'in"Allah yasa ka yi min ciki yau." Tsaki yaja mai girma kafin ya Juyo ya na kallonta sai da ya kariso gabanta. Sannan ya kausasa murya yana fadin"Ni ban isa na baki ciki ba Sultana, ina so ki sani Ubangiji shine mai komai, shi ke samar da Ciki a jikin mace sannan ya Rayar da shi daga Gudan jini zuwa ya Busa masa rai, ni din banza da na isa na ba da abunda ba ni da Hurumi a kansa? Ki saka aranki Allah ke ba da wa, kema shi zaki Roka ya baki mafi Alheri." Daga haka ya yi gaggawar Ficewa daga Dakin bayan ya Dauki wayarsa da ta watsar nan saman gado, bai jira jin wata mganarta ba. Falo ya fita ya zauna ya yi Shuru yana Tunanin Rayuwa, Sultana ta na neman ta hanaahi kwanciyar Hankali. Ya yi iya Tunaninsa ammh ya kasa gano inda ya tauye mata hakkinta. Saboda ya mamta da Tunaninta yasa ya Kira Siya har ta fara barci ya tasheta yace su yi hira. Ya tambayi su Asim tace ta baro su aciki tare da Habiba sun yi barci da Wuri, da alamun akwai su da zarin cikin Dare. Sadiq har wani gyara kwanciya ya yi a saman kujera na zaman mutum uku, Hira ya ke yi cikin Annushuwa da Farinciki da ya saba kasancewa aciki in dai yana tare da Siya. Har ga Allah bansan Assadiq na Gusau ba tunda bai gayamin ba. Hira na saki jiki ina yi masa duk da akwai gajiya tare dani tunda da Safe akwai makaranta Tp din mu sun kara mana wata daya mun samu an zo Dubamu sau biyu saura daya. Ina basa Labarin yadda su Asim ke da Farinjini a makarantar ne. Har mai makaranta daukansu ya ke yi su tafi office ko kuma in zai yi zagaye malamai har fad'a suke yi wajen daukansu ni kan nace masa bani da matsalan Renon su Asim yanzu. Sadiq na dariya yace"Ko? To shikenan nan gaba Allah ya kawo wasu yan ukun lafiya." Da Sauri nace"Astagafrullah.." Cikin yar dariya yace"Ki ma shirya, ina harin yan uku ne wannan karon" Cikin Shagwaba nace"Haba dai ni dai ka bar wannan mganar Assadiq kada ka fad'i gaban yan Amin su amsa hakan ta faru." Cikin danne Dariyansa yace"To nasan Siyata jarumace zaki iya" Ya shagala da wayar da ya ke yi baisan Fitowar Sultana ba. Sai da yaji an fizge wayar hannunsa cikin Tsananin kishi idanuwan Sultana Jajir ta saukemai daya dago ya na kallonta. Cikin mamaki yace"Miye haka? Ko baki ga ina waya ba ne? Sultana ta Duba wayar ta kunnata Haske ya bayyana. "Siya ta.." Shine sunan data gani ya kira kuma har Lokacin Tana kan layi, kishi ya gama Rufe mata ido yasa ta kara wayar a kunne ni kuma daman n sandare da mamaki tunda kunnuwana sun jiyomin muryan Assadiq yana mgana kafin na gama Tunanin tare da waye ya ke mgana naji muryan Sultana cikin Masifa ta na fadi'n"To tsohuwar kilaki, mai kwacen mijin wata macijiyar da bata ramin kanta, kin kwace min miji na kyaleki duk da haka bai isheki ba sai kuma yana tare dani ki rika kiransa kina masa barikin da kika saba ko? A fusace Sadiq ya mike yana fadin"Ke sultana bani wayata, kada ki zageta fa" Ammh sai ta koma da baya ta cigaba da chabamin manganun Tozarci da cin Mutumci ni kuma ban maida mata martani ba. Illah hakurin da na bata na kashe wayar, ina Tunanin me yasa Assadiq ya kirani yasan cewa yana tare da matarsa? Acan kuwa Sultana ta Rotsa wayarsa da kasa ransa shi kuma ya baci Haushi ya kwashe shi ya tsinketa da mari nan ta durkushe ta na kuka shi kuma ya duka yana Tattara wayarsa cikin Huci. Sultana na Dafe da kunci tace"Ni ka mara Yaya Sadiq? A fusace yace"Kirani da Abubakar dina, zai fi min da kirana da kike da yaya bana so." Cikin kuka da hawaye tace"Akan wata banzar bazawarar matarka ka mareni? Akan matar da ka sameta a sauran wasu ka tozartani? Cikin Idanuwanta ya kallah kafin yace"Eh a kan wannan bazawarar da kika raina a kanta na mareki, kuma daga yau ina so ki sani in kika Kuskura kika kara kiranta da banza sai na ci miki mutumci sunanta Hasiya ba bazawara ba, in bazaki Darajata ba a kallah ni ki bani Darajar da Allah yace ki bani, kuma gargad'ina da ke shine na rantse da wanda raina ke hannunsa in baki shiga Taitayinki dani ba sai na jefar da Rayuwarki a cikin Rayuwata sai lokacin ne zaki gane ke din banza ce a wajena." A fusace ya kwashi farfasshiyar wayarsa zai wuce cikin daki sai kuma ya dakata ya Juyo yana kallonta ya nuna ta da yatsa Lokaci daya yana Fadin"au na manta ban fad'a miki ba, ita wannan bazawarar da kike  ganin kin rainata  ta fi min ke sau Dubu wlh" Daga haka ya Buga iska fuu ya Shige dayan dakin ya Bango kofa ya bar Sultana Zaune a saman cafet ta na gunjin kuka. Tun tana kuka da karfi har ta gaji ta koma yi a sannu kanta ya fara sara mata, nan ta yi barci bata sani ba Sanyin Asuba ya tada ita taja kafafunta ta Shiga dakinta. Fuskarta ta kalla a madubi har in da ya mareta ya tasa, ita ba marin ne ya dameta ba sai da yace wai Hasiya ta fita a wajensa sau dubu, ita yanzu ashe a banza ya ke kallonta? Dakyar ta yi sallah sai kukanta ya Dawo Sabo. Ta rasa wazata tunkara gashi ta bata rawanta da Tsalle a wajen Umma. Kuma bata isa ta tunkari gidansu da wannan mganar ba kilama Babanta sai ya kara mata. Daga karshe ta kira Surayya ta na kuka ta gayamata abunda ke faruwa Saboda tasan su Sajida ba abunda suka isa su yi, tunda Sadiq ba jin mganarsu ya ke yi ba gwara Big sis din. Surayya kuma Hankalinta ya tashi jin harda duka da safiyar nan duku duku ta yi Driving zuwa gidan  a Haraban gidan ma suka hadu da Sadiq ya Dawo masallaci Tunda ya ganta yasan Sultana ce ta kirata ko d'ar bai ji ba shi daman fa ya gaji gwara a san abun yi yarinya karama bazata zo ta hanashi Zaman lafiya ba, ina bata isa ba wlh. Tare suka shiga gidan tana Tambayasan ina matar gidan? Yace shi bai sani ba ta Dubata. Ita ta shiga dakinta ta sameta ta na kuka. Sultana ganin Surayya yasa ta kara jiniyan kukanta. Dakyar ta lallasheta ta yi shuru kuma ta nuna mata wajen marin taga ya Kumbura. Duk da Sultana ta fadin duk abunda ya Faru Surayya bata tsaya anan ba ta tarasu tare tace kuma Sadiq ya yi mgana. Yace shi bazai ce komai ba in har ta bari ya yi mgana sai ta raina kanta. Abu daya ya sani ya gaji da zama da ita Tunda tana zargin baya yi mata adalci gwara ta fad'i abunda ta ke so ya yi mata kowa ya Huta. Sai Tsoro ya kama Sultana jin abunda yace ta fara kuka Dakyar Big sis ta lallashesa ya fadi laifin da take yi masa. Ya ce na farko bata darajashi, na Biyu ta raina shi na uku ta dauki wasu ta fifita sama da shi, na hudu kishinta na Hauka na Biyar ta na zarginsa da bata zama lafiya da shi. Nan fa Surayya ta yi ma Sultana fad'a Sosai ta kuma sakata ta duka ta bashi Hakuri tare da alkwarin zata bar komai da ta ke yi zata kuma gyara dakyar yace ya Hakura ammh in ta kara ya rantse da kansa zai sakata a Mota ya maidata shinkafi. Tunda ta raina Umma itama yanzu bata da kima acikin Idanuwanta. Shima Sultanan ta fadi na shi laifin maganarta daya ne baya sonta yafi son Matarsa a kanta kuma yana yin mata kaza itama baya yi mata. Mgana dai duk na zarge zarge da kishin Tsiya. Surayya dai nan shima ta nuna masa ya gyara sannan tace kada ta kara jin ya kara kai hannu Fuskar Sultana matarsa ce ba Jaka aka aura masa bq shima ya ce ya yi kuskure bazai kara ba kuma ya bata Hakuri a gaban Anty Surayya, sannan shima yace ta ja mata kunne ta daina zagin masa mata yadda bazai bari siya ta zageta ba shima bazai bari Ta zageta a gabansa ba. Nan dai Surayya ta zaunar da su gabadaya ta yi ta musu nasiha itace sai Goma na safe sannan ta koma Gidanta bayan ta tabbatar ta gyara barakan dake Tsakanin su. Ta dai yi kokarin kebewa ita da Sultana ta gayamata gaskiya ta daina Biye ma zugan kowa sannan kuma ta Rike sirrin mijinta ko Tambayanta akayi tace bakomai..sannan ta yi masa Biyayya ta daina ja inja da shi sannan ta gyara kanta da jikinta har maganin gyaran jiki tace zata aiko mata da shi don Allah ta gyara. Ta kuma yi mata alkwarin zata gyara sannan tace ta shirya taje ta ba ma Umma Hakuri, ta yi fushi da ita. A lokacin ta yi kuka ta nuna Nadamarta. Kuma tana da tabbacin in taji shawaranta bazasu kara samun matsala da Sadiq ba, in kuma bata ji ba komai zai iya Faruwa. Yanayin mganar Sadiq tasan da gaske ya ke yi ya gaji. Kuma gajiyarsa daidai ya ke da Faruwar komai. Sannan Surayya ta sakata ta karb'i lambar Hasiya a wajenta ta kirata ta bata Hakuri Hasiya tace ita bakomai bata riketa ba, kuma a gaban Sadiq din aka yi, sannan shima tace kada ya sake Doguwar waya in dai yana tare da d'aya daga cikin su Saboda a zauna lafiya. To kamar dai Abun ya Dore Sultana ta gyara ta koma kamar Farkon auransu, sai ga shi har kwana ya kara sai Ranar Monday ya koma Abuja. Sannan sun je tare ranar lahadi da Daddare ta ba ma Umma hakuri. Umma tace ta yafe itama ta kara yi mata Fad'a sosai. Kamar taga uwar bari ne tunda ko su Sajida sun kirata su ji Labari su kara zugata sai taki gayamusu komai. Ammh fa kishin Hasiya da tsanarta na nan acikin ranta sannan Babban Burinta yanzu ta samu ciki itama ta Haihu. Har ta fara damuwa auransu ya fi shekera ba ta samu ciki ba, shikuma sai yaga kamar abun ya fara taba mata Tunani sai ya koma yana lallashinta duk sanda yazo, ko kuma suka yi mgana ta waya. Yana nuna mata Haihuwa ta Allah ce itama bai manta da ita ba ta yi ta addu'a zai bata. Har fa asibiti ta saka sukaje aka auna su likita ya tabbatar da suna lafiya sannan ta yarda lafiyar kalau lokaci ne bai yi ba. Saboda ta rage damuwa yasa ya matsa mata ta siya jamb ta zana kuma ta samu Score mai kyau. Nan take ya nema mata Gurbin karatu a jami'ar Gusau. Ta fara karatu a tsangyar B.A English. Sai karatun ya fara Dauke mata Hankali da wasu abubuwan ammh kishi nan da zargi bata daina ba tadai rage da kuma nuna an yi mata ba daidai ba. Shi kuma ya sha zaunar da ita yana fad'a mata tafi Hasiya zama acikin gata, ni acan a gidan haya na ke zaune, da ire iren mganganunsa yasa ta fara Fahimtar gwara ita tunda tana cikin gidan sa ne. ******** Ni kuma a lokacin har mun gama TP mun koma makaranta muna karishe Sauran Semister mu. Su Asim na da watani bakwai a lokacin Tuni har sun fara zama, karatu yasa ban kara komawa Gusau ba Tafiya ma sau daya na yi. Amma ciwon ta ya tashi har asibiti ta kwanta mukaje na kwana daya na dawo. Koda yaushe korafin su Umma yaushe zan zo na kawo musu su Asim? Sai dai nace zan zo in sha Allahu makaranta ce ke boye ni. Assadiq yace min Siyama ta samu mijin aure lokacin Bikin zai yi daidai da mun gama jarabawa sai naje daga biki na jima acan. Assadiq bai taba gayamin zai tafi dani Abuja bayan na gama makaranta ba, na fi ma Tunanin gusau zai maidani da zama, zan so haka Tunda yanzu bani da matsala a wajen dangin mijina. Masu matsalan ma kalilan ne. Siyama a garin Gusau ta samu miji wani likita ne zata aura ba'a kuma saka Lokaci mai Tsawo ba..wattani Hudu aka saka Shiyasa Shirye shirye ya tashi Gadan gadan. Ni ma kuma ina ta shirina Tunda Assadiq yace zan jima acan daga Bikin Siyaman. Biki ya rage wata daya muka gama Jarabawar karshe muka yi bye bye da makaranta sai jiran sakamako. Assadiq ya shiryamana Tafiye tafiye a shekaran yace har Daura zamu je garin su Tahir zamu je shinkafi. Tahir an saka masa ranar aure Wata Hauwa'u zai aura yar cikin garin katsina. Ammh saboda yana gini shekara a ka saka, kuma agarin katsina zai zauna Saboda Siyasar da tafi karfi a cikin garin katsina. Turaren Wuta na siya ma Siyama Gudummuwa tare da kayan gyara na Saiwowin Dahuwar kazar gudiyo wajen Marubuciya Surayya dee, aika musu da shi na yi ta Hannun Anty Surayya Tunda itama na gayamata ingancin kayan ta fara amfani da kayan gyaran Surayya Dee takwaranta. Ku gwada ku gani kayan gyaran Surayya Dee masu kyau ne da inganci ni Hasiya tabbaci na ke baku ba yakini ba.+234 803 277 3332 Mama da kanta ta kirani ta na min godiya nace bakomai, Assadiq sai dak yaji nayi yan'uwansa abun alheri ba na gayamasa shiyasa nima daidai gwargwado ban taba neman wani abu na rasa ba. Ko su Adda Fati sai dai na Taimaka musu, ko Adda Rukayya da ta ke ganin mijinta na da hali bata kama kafata a jin dadi da saka Suturu ba. Mijinta ya sani ni yanzu na sha kwana domin mun taba haduwa kwanaki a gidan Adda Rukayya. su Anma na fama da su Asim ba ni kadai ba har ya'yana haka ya rika kallo yana mamaki Da na gaishe shi ya amsa yana kara tambayar Adda Rukayya ni ce na koma haka?. Ita ko tace nice mana ta na bashi Labarin mijina da Danginsa. Sai mamaki ya ke yi, daman abunda ka ke zaton bazai Faru ba shine ke faruwa. Labarin Haihuwata har a kunnen Sahura da yan'uwan Salisu tunda na had'u da kanwarsa. Har gidanmu na samaru da muka zauna suke zuwa tambayansu  Maman boy da gaske ne na Haihu yan Biyu? Su kuma su ka tabbatar musu. Har da karin cewa wai shima mijin nawa ya yi hadari Allah ne ya yi kwanansa na gaba. Maman salihi da ke bani Labari tace sun ce musu da gaske ne, abunda Tunda shi ya yarda ba mai yi sai Allah suna nan tare da juna cikin Soyayya. Ramatu na gayamin Salisu ya kirata a waya yace ta tura masa lambata ya Kirani tace bazata tura masa ba ni matar aure ce sai ya nuna mata Hakuri zai bani tace ai Hasiya bata rike ka a ranta ba. Ni kam in inajin Labarin nan sai naji kamar komai bai Faruwa ba, sai nake ganin abun kamar al'amara Allah Sarki Rayuwa Abubakar ne bani da Labarinsa gwara Salisu duk ana tare a anguwa daya sannan indai zan Tuna Halin Tsaka mai wuyar da na Shiga bazan manta da Salisu da Abubakar acikin Rayuwata ba. Kawayena guda Biyu da Assadiq ya Sanni da su daga Ramatu da ta kara Haihuwa kwanaki sai Safiya da Sanadin makaranta muka Kulla zumunci yayarta ta yi aure khariyya na yi mata kara sosai kamar yadda nima take yi min in Sha'anina ya tashi. Anko wajen kala uku suka Fitar akwai na walima sai na yinin biki sai kuma na Sister day. Duka kuma Assadiq ya siyamin acan kuma aka d'inkamin. Nima ta bangarena na siya Sabbin mayafai da jaka da takalmi. Sannan na Dage da Sabaya nan ina Damawa ni da yara muna sha ganin Tsotso duk ya kara Tsotesni gani daman ba auki ba. +234 706 548 1260 Cikin Lokaci na ciko na yi bul bul dani gwanin ban sha'awa. Tun ana saura Sati daya na tafi Gusau motar haya na shiga sai tashar Golf na yi Assadiq ya turamin kud'i yace Saboda yara gwara mu samu sarari. A dakin Umma na sauka kamar yadda Mijina yace. Sai dai ban san cewa itama sultana ta dawo wajen Umma da zama ba sai da naje na ganta kwance duk ta rame sai fama ta ke yi da Amai. Ashe ciki gareta kuma yana saka ta  laulayi mai zafi. Tana ganina ta fara gulma gulmace kakaro Amai da Sanabe kala kala wai ita mai ciki yara ko su Asim tuni suna hannun dangin Ubansu har Rubibin Daukansu ake yi. Kusan nice bakuwa ta farko data fara sauka dagani sai Saliha sai Anty Saddiqa. Tare dani aka yi sauran shirye shiryen su Sajida har Lokacin ba su min mgana in na gaishesu sai sun ga dama suke amsani. Ni da Umma kam sai son barka, bata kara nuna min wani Tsamgwama ballatana Tsana ba. Ya'yana ko sun zama abun so acikin Dangi, ni kaina na had'u da su Saliha da Anty surayya na shige cikin su ban maida kaina bakuwa ba. Gyaran kai da kunshi duk a Gusau na yi shi tare da su Anty Surayya. Sultana ta so ta yi, ammh ba hali duk da tanq babban kawar Amarya Laulayi ya hanata Burinta ya Cika ta samu Ciki. Iyayin da ta ke yi da wannan cikin sai wanda ya gani, tun ballatana da ta gani sai abun ya karu. Ni a dakin Umma wannan karon na sauka na barta dakinta da na sauka wanchan karon ni bata gabana. Sai dai ina gaisheta kullum da safe ta amsa tana wani yamutsa fuska. Tun kafin nazo daman an yi amarya Jere, saura kaya kawai ake kaiwa can gidan Innani na nan sai dai yanzu jikinta yaki dadi yau lafiya gobe ciwo kuma taki yarda aje asibiti, innani dai Jikin Tsufa kawai da Shekaru ne sai dai kawai Allah yasa Tafiya ta yi kyau. Mutanen shinkafi duk sun iso suma, da na cikin garin Gusau Dangin Mama. Assadiq sai ana Gobe Daurin aure ya iso da yamma, lokacin muna gidan Surayya gabadayanmu inda ake Walima. Sister Day sai ranar lahadi a gidan Amarya za'ayi yinin biki kuma a gidan Abba. Sai kirana ya yi a waya yace ya zo bai ganni ba. Nace muna wajen walima matsamin yayi sai na dawo tunda su Asim na wajen Umma sun fara kuka. Ana mangariba Anty Saddiqa ta Tukomu zuwa gida. Sultana ta rarrafa taje walimar ammh muna dawowa taga Assadiq sai ta koma ta narke ta ce nan ke mata Ciwo tace nan ne Ni dariya ma take bani a raina nace lalle yarinyar nan bata san ciki da Haihuwa ba ne shiyasa. Washegari aka Daura auran Siyama da angonta Saleem. Gida ya cika da mutane kaf dinsu ba wacce bata zo ba, mun sha ankon yinin biki mun yi kyau gwanin sha'awa. Assadiq ma yaci Fararen kaya shi da Tahir tunda ya zo masa Daurin aure Abba kuma na can da bakinsa abokan arziki irin su Alhaji Jibril da ya yi ya kusheni a wajen Abba ya kasa samun nasara. An sha Hotuna sai wansda ya gani, ni ban Tusa kaina ba sun dai sun karbi su Asim suna ta Hoto da su ni kuma ina gefe sai da Surayya ta jawoni cikinsu tana fadin nima ai na zama yar cikin Family din SS SHINKAFI. mun sha Hotuna kuma kowanne Hoto sai su ce duk na Cinye su. Ammh fa su Sajida ina shiga suka Fita daga Hoton ba kuma wanda ya Damu da su. Assadiqa ma ya yi Hoto da yan'uwansa Sultana da ta sha kwalliyarta harda makeup ta Lafe masa suna ta Hoto shi kuma yana Dauke da su Asim. Saliha ce tace nima na shiga a yi mana ni ba domin sun matsa ba, ba zan Tusa kaina ba. Zuwa la'asar aka yi haraman Tafiya da Amarya tunda an ci an koshi. Mu bamu tafi a ranar ba sai washegari Lahadi tunda za'ayi Sister Daya. Kuma abun yi yi kyau Sosai sai wanda ya gani an ci kuma an sha, sai aka kara gyara gidan Amarya mai kyau da shi  ni da da gidan Anty Surayya. Muka bar Amarya a gidan tare da Fatan Zaman lafiya na har Abada. Da daya da daya baki suka watse suka barni a gusau. Assadiq har ya koma Abuja yace sai na yi wata a gusau in yazo sai muje Shinkafi. Umma da taji Labari tace tare zamu je shinkafi itama ta kwana Biyu bata je ba, Sannan har Gummi zamu je a kai ma mallam Zakari Asim ya gansu Jin haka yasa yace shikenan na Shirya mu tafi da Umma. Sultana kuma ba Halin tace zata ga Laulayi ga makaranta dole ta na ji ta na gani muka tafi muka barta. Shinkafi muka fara zuwa can naji abun mamaki,ana ta cewa Sultana tace ita yan biyu zata Haifa. Umma tace bata sani ba, Cikin da bai yi kwari ba ne har ta san yan Biyu zata haifa? Ni kuma har a raina sai na yi mata Fatan Allah ya bata, ni bata san na gada ba ne, iyayen su Amma kakkaninsu tagwaye ne kuma asalin Zuru'rsu suna haihuwan Tagwaye Ita kuma Sultana saboda ni ne ta ke son ta haifi Tagwaye ita a dole sai ta yi kwacen son da ake yi ma ya'yana ya dawo a kanta. Tab ni ko a raina nace iska na wahalar da mai kayan kara.! *Janafty* *TMWB3K016* *TMW is a paid Novel, Pay 500 for regular or VIP N1K, Via 0552179550 Jamila Umar Gt bank, 09069067488* https://chat.whatsapp.com/IhAz8h8nRy250ZnGGXwM65 Kwana Biyar muka yi a shinkafi Daganan muka wuce Gummi ni da Umma, naji dadin garin Shinkafi sosai ba in da Umma ba ta kaini ba. Sai dai kiji ana nuna ni ana fad'in nice matar da Abubakar ya aura a Boye kafin ya auri Sultana. Kuma ba tsamgwama ba Wulakanci gidan baba Sammani muka sauka nan muka yi kwanakin mu har muka tafi, Su Asim sun sha jagwalgwala kamar me, ba su wannan gidan ba su wannan gidan. Da zamu taho kuma suka had'o min da kayan arziki, ni Alkalama suka bani da shinkafar Tuwo sai gyad'a aya da sauran tarkace sukace na had'a ma su Asim kunu ne, daga ganin yadda jikinsu ya yi fresh da kiba kunin alkalama na ke ba su. A gummi ma mun samu kyakyawan Tarba Mallam zakari daman tun zuwan mu na Farko nasan halin kirkinsa. Ya yi ta kara ce ma Umma ko ita fa? Ganin mu tare kad'ai ya kara sanyaya masa rai ya yi ta fara'a da murna ni kaina ya yi ta sakamin albarka tare da Nasihun zaman duniya. Matansa ma alhamdulillah sun karramamu, Barin ma Inna mero ita Umma mahaifiyata ta Dade da rasuwa sai sauran matan mallam da yan'uwanta masu aure a garin duka mun ziyarcesu sun gani sun kuma ga su Asim sun saka albarka. Anan dai kwana hud'u muka yi muka Dawo gida, Daura ne bamu samu zuwa ba, Assadiq yace na bari in Bikin Tahir ya tashi sai mu tafi gabadaya Umma na jin haka tace itama da Farko da taji zamu je sai ta ce mu bari mana Tunda ga Bikin Atrahiru na matsowa. Wasa wasa fa na share watanni biyu da wani abu a garin Gusau kuma a dakin Umma Tunda har Lokacin Assadiq bai ce min na koma ba, ni kuma ban gayamssa na gaji da zama zan koma ba. Daman kuma ya fad'amin na dauki kaya masu yawa tunda zan jima acan, sai dai jimawar ne ban dauka zata kai wattanin haka ba. Sai da na zauna da Umma na kara ganin Tabbacin Abunda Anty Surayya da Assadiq ke fad'amin a baya a kanta. Hakuri, sanin ya kamata da kyakyawan zuciya Umma ta na da kirki sosai da ba ta da bakinciki ko kyashi na yi mata Uzuri ya fi sau Saba'in Tunda na Fahimeta. Na kuma san a irin  Labarina da yanayin auren mu ya kasance da Assadiq a matsayinta na uwa na Tsammaci abunda yafi haka Daga bangarenta. Duk da ba zama muke yi mu yi Hira sosai ba daga gaisuwa sai abunda ba'a rasa ba. Mganar su Asim ma tafi had'amu Tunda ni dai tun zuwana ban san wahalarsu ba Umma ce da Mama sai Farida ke ta wahala da su ni kam sai in suna kuka a kawomin su na basu Nono, sai kuma in zamu kwanta da Daddare. Ni iyakata in na tashi da Safe, mai Musu aikace aikace sai da rana take zuwa kafin tazo na gama gyara bangaren Umma tas tun Tana cewa na bari har tagaji ta kyaleni. Ni na riga na saba da aiki Shiyasa ban iya zama, hatta Abun karyawa da Safe ni na kan yi, Har Abba ya sha cin girki na Wani lokacin da rana ne mai aikin kan Dafa ammh har na Dare in ya kare da naga Umma zata Daura sai na karb'a na Dafa. Sultana kafin ta koma sai dai taci ta kwanta ita a dole mai laulayin ciki Alhalin in hira ne da yini ta na rike da waya ta iya shi. Tayi wani abu da ya bani mamaki bayan Bikin Siyama. Tunda taga Assadiq ya dawo bayan Bikin ta mike ta nuna taji sauki ta warke, Umma tace ya dauketa su koma Gidansu. A lokacim ban Fahimci abunda ta ke nufi ba sai da ya gama kwanakinsa ya tafi tsakanina da shi sai gaisuwa ko tambaya game da abunda yara ke Bukata. Ranar da ya koma Abuja ta kwaso kayanta ta dawo ma Umma wai bata son kamshin gidan sannan komai taci sai tayi amai ta barta ta zauna a wajenta kafin Assadiq ya dawo. Mamaki ya kamani hatta Umma sai da ta Fahimceta kuma daga haka ta Samu sara da ya dawo zata koma gidanta yana barin garin zata Dawo wajen Umma har sai da Umma ta mata Fata fata tace ta zauna gidan mijinta bata son iskanci in abinci ne za'a rika aika mata da shi. Tunda tana gani ta ji sauki har makaranta ta na zuwa ta kuma yini waya da charting sai taga mijinta ya Dawo ta narke masa su koma gidansu. Kuma duk Saboda kada ya samu Sararin kebewa dani ne tunda ina Gaban Umma. Ni bata ma sani ba, ko yana gari ban cika nuna kwad'ayina a kansa ba. Wani lokacin ma nafi zama a bangaren innani da Rana tunda yanzu jikin Innani ya fara saki tafiya ma dakyar ta ke yi ko da Sandar bata cika ma yawan fitowa ba. Jikin tsufa sannan ga Shekaru shiyasa yau lafiya gobe Ciwo ga shi bata san asibiti sai dai Likita Abba ya Dauka ya na zuwa gida ya na Dubata. Yanzu duk hiran Innani ba shi, sai dai ranar da taji jikinta da karfi zata saka akawo mata su Asim ta Biye musu su yi ta wassani, nima muna zence da ita Sosai yanayinta kad'ai in ka kallah zaka san Innani shekaru sun yi nisa duk da bata cikin wahala ammh jikinta ya fara saki na alamun shekaru ya fara tafiya. Kuma ni in dai yana gari iyakata da shi mu gaisa shine ma ya yi ta kirana a waya yana son ganina kuma nasan Dalili saboda kada ma ya Rutsani a daki yasa ban cika zama a daki ba, in ba Falon Umma ba ina bangaren Innani Tare da Farida ina tayata kula da Innani da ta zama sai dai a lallab'a yanzu. Sau d'aya ya tab'a min Magiya na bishi muka je Hotel muka kad'aice da sunan mun je gidan matar abokinsa kuma Tunda muka dawo naga kamar Umma ta Fahimci abunda ya Faru ban kara yarda na bisa ba. Tunda dai ni kaina ban taba jin Labarin a garin gusau yana da wani aboki ba, d'aya na sani shine Tahir kowama shi ya sani. Ko ya yi min magiya ba na Biye masa zuwansa na karshe har cewa ya yi na koma gidansa na zauna tare da Sultana kafin na koma zariya. Ba halina ba ne yi masa gaddama ammh na tuna yadda na wulakanta ne a baya da ya kai ni Shiyasa da Sauri nace masa bazani ba, ya bar mata gidanta nima ina jin dad'in zama tare da Umma. Kuma nace masa Anty Surayya ta na zuwa Lokaci bayan Lokaci ita da su Anty Sakeena. Tunda bayan bikin Siyama duk naje gidajensu mun kara gaisawa, gidan su Sajida ne ban kara marmarin komawa ba. Hatta gidansu mama naje, ni fa yanzu a gusau in da ban je ba kad'an ne sosai nasan gari. A lokacin kallo na ya yi kafin yace"Siya yanzu ke sanin gari yafi miki Bukatun  mijin ki? Ni ne fa Assadiq din ki? Ina marairaicewa nace"Ka yi hakuri To, ba haka ba ne kaga ina tare da Umma kuma naga kana da wata matar ba gauro ka ke ba." Kallona ya yi na wani Lokaci kafin yace"Shikenan, tunda an hanani Babba, to ko sumbata ne a rika bari ina Rage zafi da shi." Ban hanashi ba nima na taimaka masa muka samu natsuwa da gangar jikin juna. Kuma a bangarensa ne abun ya faru Ranar ma Umma na cikin Dakinta kanta ke ciwo ta samu ta sha mgani ta kwanta shine ya jani bangarensa. Yaso ma na rika zuwa bangaren nasa in yana gari saboda ya rika Samun Abunda ya ke so. Ni kuma kunya da kuma ganin girman Lamarin a gidan surukai yasa na ki yarda da mganarsa. Duk iya wattanin da na yi a Gusau sultana na bar miji ta na cin karanta ba Babbaka. Ban taba nuna Damuwata ba, kuma ko sau d'aya ban taba yi ma Assadiq korafin nagaji ko zan koma Zariya ba. Kwatsam dawowar nan da ya yi lokacin ina da wata uku a gusau su Asim har sun fara rarrafe har kuma suna kama abu su Tsaya. Wattaninsu goma kenan  suna samun shan madara kuma Umma ta kara sawa mun dage ma basu kunin ne yanzu ko Babansu sai da Nishi ya ke d'agasu. Gashi har sun fara Haddace kowa na gidan in suka ga Abba ko Assadiq sun rika mika hannu kenan suna gwaranci haka suke yi ma Umma da Mama da farida su wai sun san su. Ita Umma bata damu da zama na ba, bataki ma na zauna tare da ita ba saboda bata san yin nesa da jikokinta. Bansan cewa Abba ya kirasa a waya ya yi masa mgamar bai kyauta ba, in a nan zan cigaba da zama nima a nema min muhallin zama na kamar Sultana. Har da Umma ya yi mganar ita kuma ta nuna masa in ma hakame sai dai na zauna a bangaren Sadiq din tunda ba kowa aciki yanzu, Saboda yara sun saba da nan d'in. Abba kuma yace a bari mijina ya yanke abunda ya ke ganin yafi masa Sauki. Ni duk bansan anyi haka ba sai da Asaadiq ya zo washegarin da ya dawo da yammah ya sameni a cikin dakin da nake kwana ina gyara kayan su Asim da aka wanke a kuma goge musu. Bayan mun gaisa shi da kanshi ya Dauko Labarin abunda ya faru tunda Farko har karshe. Ya cike da bani Umarnin na Shirya zan koma Zariya na yi parking d'in sauran kaya na kuma yi sallama da yan'uwana Abuja zai tafi dani Gabadaya. Cikin mamaki na Bud'e ido kafin yace"Ni kuma? Abuja? Kai Tsaye ya gy'adamin kai, alamun Tabbacin haka sannan da bakinsa ya ke fad'amim Umma taso na zauna a bangarensa saboda su Asim. Ni dai ban ce komai ba Tunda mgana na Hannunsa bayan ya tafi ne Umma ta kirani har Dakinta itama ta gayamin Bukatar mijina. Kaina na kasa nace"Umma tunda kina so mu zauna anan din, sai mu zauna shi sai ya tafi da Sultana." Umma tace"Da ke yace zai tafi Hasiya, ita Sultana yace ta na makaranta. Bakomai fatana kawai ki kula da su Asim sosai." Sai naji kwalla sun cika Idona cikin Sauri nace"Umma to dukkan mu ya barmu anan mana, ni kaina bana son zuwa ko'ina na barki." Umma ta yi wani mirmishi kafin tace"Kada ki damu dani, ai ya kawo min Hujjojinsa kuma na gamsu da su kije ki fara shiri yace sai kin koma ta Zariya ko? Sai na gyad'a mata kai cikin wani yanayi, mun dad'e zaune kowa na tunani acikin ransa kafin ta sallameni na koma dakin da na sauka. Sai kuma naji bana son Tafiya Allah Sarki bako Rab'a. Kuma daman ni komawata Zariya yazo min adaidai, Saboda Safiya ta kirani tace an fara Sreening din Result dinmu tun tuni ni ba na nan, sai na tabbatar mata ina nan dawowa in sha Allahu cikin satin da zai shiga. Sai gashi kafin kace me, mganar komawata Abuja ya shiga kunnuwan duka yan'uwan Sadiq. Ban sani ba ashe tunda Assadiq ya Furtama Sultana zai tafi dani Abuja ta Buga Tsalle tace bai isa ba sai dai ya Fara tafiya da ita in kuma ba haka ba, bata yarda nima ya tafi dani ba. Ni bansan ma sun yi haka ba, sai a bakin Anty Surayya na ke ji sanda ta ke maimaita Umma. Itama Umma ai su sajida sun zo suna ta kananun maganganun bai kamata ta yi shuru ba, a dalci Sultana ce ya kamata ta bi shi Abuja bani ba. Umma dai ta yi banza da su ta yi kamar bata ji ba, Su kuma suka kara Zuga sultana da idanuwanta ya Rufe ta mamta cewa ita yanzu karatu ta ke yi, a yadda ta nuna ma zata ijiye karatun ta bisa saboda ni kada naje. Ni dai ban bi ta kan kowa ba na gama duka shirina Tunda yace a wannan Satin in yazo zai maidani Zariya da kansa. Kuma har ga Allah sai da Tafiyar ta taso ya ke bani Labarin a ma'aikatansu  suka ba su Gida da Mota shi dai bai karb'i mota ba, gida kawai ya karb'a duk wata za'a rika Cirewa acikin albashinsa sannan Estate ne kamfanin ya gina musu na ma'aikantan su ne. Ranar Jumma'a Assadiq ya Dawo bai kuma zo gidan ba sai da Safe gidansa ya sauka. Sai dai tare da Sultana suka zo, ni ina wanka Umma ta yi ta lekoni su Asim suna wajen Abba daman tun safe Umma ke wankesu tas ta shirya a bunta. Sannan Tun ina wankan naji ana ta kiran wayata, ina fitowa naga Assadiq ne sai na bi bayan kiranshi tunda mun yi da shi yau Asabar zamu wuce Zariya ya kwana lahadi, litini da Safe ya koma Abuja zai barni sati Biyu na gama da makaramta da sallama da Yan'uwana sannan sai yazo ya Daukeni. Yana daukan kirana ko gaisuwata bai amsa ba yace na zo bangaren Abba yanzu. Sai na fara Tunanin Ko lafiya? Ina cikin Tararradin abunda ya Faru na Shirya cikin Wata bakar Abaya na Maryam's Epytian Abaya sai na yi amfani da wani purple din Hijabi. Ina zuwa sai naga Sultana Fuskar nan nata duk ta jeme saboda kuka sannan ga ciki tunda har ya fito duk Kishi da zargi bai barta ta yi wani kumari ba. Gefe na zauna a kasa ina gaida Abba su Asim na ganina suka fara zillo ya Sake su yana fadin"Sun ga mamansu zasu gujeni" Mirmishi kawai nayi ban yi mgana ba, ko da suka zo kusa dani ban dauke su na, Mama ce da ta shigo daga baya ta Dauki Asif, Umma kuma ta Dauki Asim suka rikesu a jikinsu suna musu wasa. Assadiq na kallah Fuskarsa ba Fara'a mun had'a ido da shi, har sau biyu banga ya sakarmin fuska ba. Sai dai da na yi masa mirmishi kad'an ya kuma maidamin da na Fatar baki. Abba ne ya katse shurun da kallon Sadiq yana fadin"Magajin gida ne ya kirani da Asuba yace zai zo tare da Sultana yana son zai yi mgana da mu tare da matansa gabadaya Saboda warware wata matsala." Ya fad'a kafin ya dagata yana kara kallon Sadiq da ya yi shuru bai yi mgana ba. Umma tace"To Allah yasa lafiya? Sadiq ya sauke Numfashin bacin rai kafin ya nuna Sultana yana fad'in"Itace zata jawo in ma matsalar ce zata faru Umma" Cikin mamaki Umma tace"Topha me ya faru ne? Ya gyara zama yana fadin"Kan zencen Tafiya da Siya Abuja ne, tunda na gayamata ta hana kanta sukuni wai ko na tafi da ita ko kuma duka bazan tafi da ko d'aya acikin su ba. Umma ban taba fad'a muku wani abu game da abubuwan da Sultana ke yi min ba, zaki tuna wani zuwa da Hasiya tayi nace ta sauka a gidana? Umma ta gyad'a kai alamun ta tuna shi kuma ya Cigaba da fadin"To Umma wulalanci ta yi min dagani har Siya, shiyasa washegari bayan na koma nace ta koma wajen ki ta zauna Sultana ta ce gida gidanta ne Tunda da sunanta Abba ya bani gida, tundaga Lokacin na saka ma raina Hasiya ba zata kara zuwa gidanta da sunan ta zauna ba, sannan Lokacin da ma'aikantan mu suka yi mana mganar gida, na so na yi ma Sultana mganar zan tafi da ita Abuja Saboda ina da mata Biyu, bai kamata na rika zama ni kadai acan ba, kuma Dalilina alokacin Saboda Hasiya na karatu itama kuma ba ta yi, har ga Allah da Farko ita na yi niyar kaiwa Abuja ta zauna Saboda nasan halinta na Zargin tsiya da nuna ana mata ba daidai ba. Itakuma Siya zata dawo gusau ta zauna kusa da ku sai na rika zuwa ina ganinta Abba nasan ko a daji na ce Siya taje ta zauna na rantse Abba bazata taba yi min gaddama ba, ballatana yau ace ta Turkeni ta na son  jin Ba'asi. Nasan halinta Shiyasa na zabi tafiya da Sultana da Farko, ammh Saboda ta na Daukam zugan su Sajida sun kitsa mata Siya na karatu itama ta matsamin sai ta koma makaranta ni kuma tana gayamin nace shikenan Tunda haka ta ke so a lokacin na so ne sai ta koma can na nema mata Jami'r Abuja, sai kuma ba ta Fahimta ba tafi Daukan mgangansu munafukan su Sajida sama da tawa mganar, Shiyasa bayan an gama gina gidajen an bamu key na yanke shaawaran tafiya da Siya Tunda tagama karatunta, ita kuma ta zauna a gidanta na nan tare daku ta Cigaba da karatunta ina zuwa ina ganinta a wata sau daya in sha Allahu." Abba da su Umma suka yi shuru suna jinjina mganganun Sadiq. Sultana kuma sai kuka tana fadin"Ni ai baka gayamin Abuja zan koma tare da kai ba, in da ka gayamin da ban shiga makarantar ba kuma yanzu ma bata baci ba ana Transfer." Kai Tsaye Sadiq yace"Haka su Munafukan suka kitsa miki? Cikin kuka tace"ni wlh ba wanda ya ke zugani na ran.." Umma ta katseta da fadin"Karya kike yi kuma anan Sultana, ai Sajida da Sadiya manyan banza ne marasa Tunani, nasan komai duk zuwa gidanki da suke yi suna Dora ki kan mgamganun banza. Ta koma ta na kallon Sadiq kafin tace"Hukuncin da ka yanke ya yi daidai magajin gida, Hasiya ta koma wajenka da zama ita kuma ta zauna a gidan da tace da sunanta aka Si ya." Mama tace"To ban da sakarcin Sultana, Hasiyar mai sanyin hali ma ba ta da girman ki in da kin kwantar da hankali lafiya kalau za su zauna." Umma ta yi Tsaki kafin tace"Ai ko ta kwantar su Sajida ba za su kyaleta ba, Abban Siyama ka kirasu ka ci mutumcin su in ba haka ba sai sun raba auran Magajin gida da Sultana da Shiga da Fitan su." Sadiq yace"Umma gwara su kashe mata auran kila ta yi hankali, ni ban mata iyakata da su ba yan'uwanta ne tunda sun fini Daraja a wajenta Fine, ni ne dai na yi musu iyaka da Matata da Rayuwa kuma na basu Lokaci ne suka kara Cikani duk sai sun kara Rena kansu." Abba ya yi shuru kafin yace"basu bar Abunda suke yi ba kenan? Ku kyaleni da su, ke kuma Sultana ki yi hakuri ki bi umarnin mijin ki kin ji ko? Sultana ta rushe da kuka tana Fadin"Abba ni tare da shi na ke son na zauna, ina fama da laulayi mai zafi ba na iya barci ni kad'ai" Umma ta saki baki tana kallon Sultana ita da Mama. Sadiq kuma ko kallo bata ishesa ba yasan halinta ni kaina na kasa ina mamakin makirci irin na Sultana. Kai Tsaye Abba yace"Ki dawo wajen Umanki, daman ai wajenta ki ke in baya gari ko? Umma tace"Sosai kuma muna nan ai zamu kula da ita, renon cikin ma duk a dakina ta yi jinyar kuma ai tare da Hasiyar da ta tsana muka yi mata Wahala" Sai kuma ta kara saka kuka har da wiwi kamar karamar yarinya Abba ya koma ya lallashinta. Ta na kuka tana fadin"Abba to kace masa ya tafi tare dani, in na kwana Biyu sai na dawo." Kafin Abba ya yi mgana Sadiq ya yi saurin taran Numfaahinta da cewa"Kinsan Allah ko da bakunta bazan tafi da ke ba. Abuja gidan Siya ne ke kuma ga gidan nan a gusau kamar yadda kikace da sunan ki Abba ya bani gidan, itama da sunanta na karb'i gidan saboda haka ki zauna a gidanki itama ta zauna ana ta gidan. Iya adalci da san zan yi miki kenan , kuma kinga ban rabaki da masu baki Shawara ba sai ki ba da Himma." Abba ya jim kafin yace"Sultana ki yi hakuri ki zauna saboda karatun ki." Umma tace"Kada ma Allah yasa ta Hakuran, kana wani bata Hakuri " Abba yace"Salamatu komai a sannu ake bi." Ina zaune na gyara zama ina Fad'in"Abba ni na hakura sai na zauna anan din ya tafi da ita." Sultana na jin haka ta daina kuka, Abba kuma sai ya yi shuru bai yi mgana ba. Kaina na kasa ammh nasan ina shan Harara wajem Assadiq Umma ce tayi karaf tace"Hasiya tare zaku tafi, kai Tashi kaje ka shirya ku zo ku tafi ba ko ba Zariya kace zaku tafi ba yau? A sannu yace'Eh zan kaita can saboda akwai Sreening din da zatayi a makaranta sai kuma sallama da yan'uwa sati biyu dai nace zan koma na Dauketa zuwa can." Umma tace"Hakan ya yi, Allah ya tsare maza ka tashi kaje ka Shirya kada ku yi yamma, ita kuma wannan kabar mana ita anan." Sultana ta kara saka kuka tana Fadin"Don Allah Umma ki ce ya tafi dani." Umma tace"Bazan ce ba, da kike zaune anan wani abu ya cinyeki? Ko duk baki san da haka ba ne sai yanzu." Sultana ta yi shuru ta kasa mgana, Saboda ita kishinta da bakincikinta Zai tafi da ne zai je ya bani duniya ban da ita, ita kuma zai barta anan sai yaga dama yazo ya ganta. Haka su Sajida suka kitsa mata, tare da bata Shawaran ta yi ta rigima tace bata yarda ba in yace karatu tace ai za'a iya Transfer indai ya nace zai tafi da Hasiya to itama tace sai ta je, Daga karshe sai da ya fasa tafiya da kowacce Shiyasa ta hanashi zaman Lafiya tun jiya da ya sauka a garin ta ke masa rigimar ita ta fasa karatu tare za su koma Abuja, shi kuma yace bata isa ba nan ne gidanta anan zata cigaba da zama. Sadiq kuma Tuni ya bi umarnin Umma ya fice abunsa bayan ya gama Hararata kamar Idanuwansa za su fad'o, ni kuma na kauda kai ni na yi hakane Saboda a samu masalaha ni bani da damuwa su je can ni sai na zauna anan tare da su Umma. Allah na Tuba wani Dare ne jemage bai gani ba? Ai sai dai daran mutuwarsa. Abba kuma ya Cigaba da fad'a akan su Sajida Mama ce ta kara da cewa"ai ni ko su Salima nace su fita sha'anin shiga abunda ba ruwansu, kada su je  su ja da ikon Ubangiji." Umma tace"Suma ki kyalesu lokaci suke jira, duniya zata koya musu hankali, ko ni da na haifi Sadiq din na saki nace Allah yasa albarka to su kuma Munafunci me suke ta kai kawo a kansa? Ni dai duk ina zaune ina jinsu, Sultana kuma na ta jan majina ta na Shesshekan kuka, Umma ta kalleni tace na tashi naje na shirya tunda zamu kama hanya ne. Abba ma yace haka ya kamata Kada magajin gida yazo yana jirana. Nima Umarninsu na bi na koma Bangaren Umma na cigaba da shiryawa. Can sai ga Sultanan ta Shigo bangaren Umma, ta kuma bi ni har cikin Dakin da na sauka ta iskeni na gama had'a kaya na da na su Asim gabadaya. Assadiq kawai na ke jira ko sallama bata yi ba haka ta shigo kanta Tsaye. Na dago ina kallonta cikin mamaki ammh dai ban yi mgana ba. Sai na maida kaina kan wayata na Bude data muna Chart da Safiya rokonta na ke yi, ta taimaka in na dawo ta rakani cikin makaranta na yi Screening. Ganin haka yasa ta tsaya a gaba na rike da kugu tana fad'in"Dole ki kalleni ki watsar mana, kinsan dai nafi karfin ki nesa ba kusa ba ni a Budurwa Yaya Sadiq ya aure ni ke fa? Bazawara sauran wani, kuma ma kin ji kunya mai kwacen mijin wasu kawai." Ta karishe fad'a cikin Rashin kunya, ina jinta sai dai ban tanka mata ba. Mirmishi kawai na yi na dago ina kallonta kafin nace"To nagode sosai." Na maida kaina kan wayata a karo na Biyu. Sai ta ji haushin ban Biye mata ba, cikin kara Tusamin haushi tace"Uhm ki kara ma Bokan ki kud'i, tunda aikinsa ya yi kyau ga shi Yaya Sadiq zai tafi dake Abuja, sai dai ina so ki sani wlh Tallahi yana can ne ammh zuciyarsa na tare dani, in a baya kina Fariyan saboda ya'yan da kika haifa ne nima cikin gareni kuma nima in sha Allahu yan Biyu zan haifa sai naga karyan Tsiya, har Umma da ke sonki yanzu sai ta daina da ke da ya'yanki dama a rashin uwar daki ta yi na kishiya." Saboda na kara Tusa mata haushi sai na kara Dagowa ina fad'in"Allah ya baki yan uku ma in dai Alheri ne ina miki Fatan haka." Ta murgud'amin baki lokaci daya ta na shafa cikin jikinta tace"Ohon miki dai, kyaji da munafunciki." "SULTANA..!" Mukaji muryan Assadiq daga sama a tare muka juya muna kallonsa yana Tsaye a kofar dakin sanye da Shadda Tazarce har da hulansa na bakar Dara. Bamu da masaniyar ya dad'e a wajen, kuma yaji duka maganganun Sultana ko daga yadda ya ke bin Sultana da wani kallo na zaki gane kuran ki. Shigowa dakin ya yi a Fusace lokaci d'aya yana fad'in"Sannu rasa kunye beran tanka, nace sannu da aiki." Kanta na kasa ta fara fiki fiki da ido na alamun bata da gaskiya. Ni kuma muryata a kasa nace"Sannu da zuwa.' Kallo daya ya yi min ya kauda kai cikin kaushin murya  ya kalli Sultana Lokaci d'aya yana fadin"Kada ki manta ba ke na fara Aura ba, ita na fara aura kuma a bisa al'ada itace Uwargida tana gaba da ke a wajena sannan a shekaru ma tana gaba da ke, ban ce ki sota ba, saboda daman ba ke ce daman ya dace ki sota ba. Ni ne ya dace da na sonta Tunda ni na ijiyeta. Ammh ki sani ya zame miki Dole ki koyi girmamata matukar kina son zama lafiya tare dani, in kuma baki so ki Cigaba da tozarta ta, ni kuma na yi alkwarin kare darajarku gabadayan ku, bazan kuma lamunci d'aya na cin mutumci d'aya ba." Ya karishe fad'a yana nuna Sultana da yatsa. Cikin gwaron Numfashi ta kwaso magana ya dakatar da ita da cewa" Bana son jin komai, na riga naji komai malama, ki fita ki bama mutane waje kawai." Ya fad'a ya na nuna mata Hanyar Fita, ai sai gata sumu sumu ta fice ta na wani sunne kai kamar mutuniyar kwarai. Ganin yadda ya Harzuka yasa na kallesa ina fad"in"Ka yi hakuri Assadiq" Cikin kuramin ido yace"Ba hakuri zaki bani, ke ce zan gayama gaskiya ni ban ce ki zauna tana miki tozarcin da taga dama ba, ki rike girman ki yadda zata gane kina gaba da ita." Kai na gyad'a kafin nace"In sha Allahu, ni ban ma Biyre mata ba." Kai Tsaye yace"Kin yi kyan kai, kayan kin gama had'awa? Ya fad'a yana kallon akwatuna  da ke tsakar dakin, sai na gyada masa kai sannan nace masa Eh. Bai ce komai ba ya kwashi akwatunan zuwa Haraban gidan Lokaci d'aya yana cemin na shirya yanzu zamu tafi. Ganin tafiyar da gaske gaske tafiyar ne sai duk jikina ya yi sanyi, Na je bangaren Innani na yi mata sallama ta rike hannuna ta na fadin"Yar nan ina jin dadin zama da ke kuma zaki tafi? Farida na gefe tace"Innani kuma Abuja fa Anty Hasiya zata koma inda Yaya Sadiq ya ke aiki." Innani tace"Shi magajin gida can Habujan zai tafi da ke? Sai na gyada mata kai kafin nace"Eh Innani haka yace" Innani ta ja numfashi zata yi mgana sai ga Assadiq ya shigo tare da su Asim dama nace ya karbo su su yi sallama da Innani. Hannuna ta saki ta rike nasu tunda Assadiq ya zauna a gabanta ya rike mata su. Sai ga Innani na hawaye ta na shafa kansu, suma kamar sun sani suna ta jan hannunta. Innani ta kalli Assadiq kafin tace"Tare zaku tafi da su can Habujan ne magajin gida?. Cikin Sauri yace"In sha Allahu, ,Ammh yanzu Zariya zan kaita akwai abunda zata karisa sai zuwa nan da Sati biyu zan koma na Dauketa mu koma can gabadaya." Innani tayi shuru kafin tace"ita sulsana nan zaka barta kenan? Yace"Eh innani zata zauna tare da ku, zan rika zuwa ina ganin ku in sha Allahu." Cikin gamsuwa Innani ta jijjiga kai kafin tace"Shikenan, da dai zaka yi hakuri ka bar min yan yara nan suna Debemin kewa magajin gida." Assadiq ya yi mirmishi kafin yace"Innani ai suna shan Nono, ammh ki yi hakuri na yi miki alkwarin in aka yayesu nan gidan za su dawo hannun Umma." Sai Innani taji dadi ta rika shafa kansu tana saka musu albarka. Harda 500 ta kwance a hannun zaninta ta ba su, nima ta na ta sakamin albarka. Har sai da Assadiq yace"Innani kwata kwata yanzu kin daina sakamin albarki d'in nan." Innani na gyara gilashinta tace"Ai yarinyar nan sai dai Allah ya saka mata, nan ta ke zama tare dani duk abunda na ke bukata shi ta ke yi min dole kaji ina saka mata albarka matar taka yar kirki ce, ka riketa Amana da gaskiya Allah ya yi muku albarka gabadaya ya baku zaman lafiya da Zuru'a dayyiba, ya kuma raya muku ya'yanku cikin Addinin musulunci ya Had'a maka kan matanka gabadaya." Ni da shi muke ta amsawa da Ameen Ameen. Sai da na yi hawaye da Innani ke ta fad'in"Allah yasa mu gana.". Ni kuma sai nace"In sha Allahu akwai rabon gwanawa a gaba Innani." Ba ni kad'ai na yi kuka ba har Umma da Mama sai da suka yi hawaye Anty Surayya ma sai ta zo muka yi sallama Umma ta had'amin sha tara na arziki kaya sabbi ta dinkamin su Asim kuma kaya sai dai su ba ma wasu, ga kayan wasa sannan Umma ta ce min duk abunda nake Bukata na yi mata mgana. Abba kuma ni da su Asim kyautar 50k ya yi mana, ina ta godiya ina hawaye Asim ya fara kuka Asif ya kama kamar su san tafiya zamu yi, Allah Sarki har muka dauki hanyar Tafiya kuka suke yi sai dakyar suka yi shuru bayan na basu Nono na kuma had'a musu da madara Sultana bata bani mamaki ba, ko da zamu tafi kowa ya fito ammh ita ko lekowa ta na shashen Umma kishinta baya Boyuwa a kaina. Sai da muka yi nisa ne Assadiq ya kalleni yana fadin"Siya kada ki karamin abunda kika yi min yau, ba na so, nace ga Hukumcin da na yanke ke kuma ki ce a'a. Ban san ki da Gaddama ko ja'in ja ba." Kai Tsaye na amsa laifina na kuma ba shi hakuri, shima kuma yace ya yafemin Muma tafe muna hira su Asim daga kuka sai barci, tun da safe daman na kira Adda Fati nace Habiba taje gida ta karbi key hannun maman Suhailat ta gyaramin daki sannan ta yi min girki yau zamu dawo tare da Assadiq. Ina ga kuma da Sassafe ta je, domin muna isa wajen biyu saura na rana muka iske ko'ina tas da shi har girkin ta gama yana tashin kamshi. Maman suhailat bata nan taje kano sai yarta ne ke gidan Ummi kuma ta na makaranta. Duk sai naga dakina ya Sauyamin, wattani uku ba kwana uku ba ne. Habiba nata santin su Asim sun girma sun zama manya ga wayau sannan taga har sun fara tatan tafiya. Ba ta dade ba, tana ganin mun dawo ta shirya ta tafi bayan Assadiq ya bata 2k yace ta Hau mashin. Muna yi sallah ban ko tsaya cin abinci ba na kira su Umma na ce mun sauka lafiya. Anty Surayya ma na kirata na kara mata godiya ta bani kayan kwaliya da dogayen Riguna da Maryam's Egyptian Abaya. Ranar Saboda gajiya yini muka yi a daki da daddare ne ya fita ya siyo mana kaza da Tsire muka ci tare da shan Youghourt muka koma muka kwanta sai dai mun ci Amarcin wannan Daren ni da Assadiq an dad'e daman ba'a had'u ba. Sannan ko da ni ke can ban yada manganunan gyara na Surayya Dee ba, na ma gani a status dinta tace zata Fara Dahuwar kaza na yi mata mgana ina so. Kafin tafiyarmu Abuja zata aikomin da shi, in ma na koma can duk ana tare tunda dai na aminta da ingancin kayanta suna da kyau da Tasiri sannan su dad'e a jikin mace ba su daina aiki ba. +234 803 277 3332 Sai washegari maman suhailat ta dawo ta zo har daki tana min maraba da sauka tace tayi kewana ni da su Asim. Na dibi kayan kwalliya na bama yarta ita kuma na bata atamfa cikin wad'anda Umma ta bani ta na ta godiya. Ban fita ko'ina ba tunda Assadiq na nan waya kawai muka yi da Adda Fati sai Ramatu da nace musu na dawo. Sai Litini da Safe Assadiq ya tafi da niyar sai bayan Sati biyu zai Dawo ya tafi dani. Nayi masa maganar kayan daki yace na barsu anan acan Abuja komai na kayan more rayuwa an saka bani da matsalan komai, kl daki kuma zai kara Biyan haya na shekara, in na zo garin zan samu wajen sauka. Shi da ya ke yanzu ba shi da wani abu da garin Zariya ni ce daman kuma yanzu zan koma kusa da shi. Sai Masters kuma tuni ya gama project ne ma yaso ya bashi matsala ammh daga baya ya shawo kan matsalan. Saboda Hakkin Zaman tare Maman suhailat da Ummi na fara gayama zan koma Abuja, suka yi min Fatan alheri. Maman suhailat kuma tace zatayi kewar mu ni da Asim. Adda Fati kuma da kaina naje na gayamata ranar da naje na kaimata Tsabaranta ita da Habiba. Ta tayani murna kwarai da gaske Adda Rukayya kuma sai a waya na gayamata. Ta kwashi gud'a kafin tace"Allahu Akbar yau ga Hasiyan Amma a garin Habuja." Ina ta Dariya, haka ma Ramatu ta yi da tazo min sannu da zuwa na gayamata suna ta cewa mahakurci mawadaci. Ina shirina a sannu sannu sannan naje gidan su Safiya itama na kai mata Kayan kwalliya na gaida mamansu, daganan kuma ta rakani makaranta na fara Sreenning. Kuma Alhamdulillah kwana hudu na yi muna zuwa ma gama gabadaya sai Jiran sakamako.. Itama tamin murna jin zan bi mijina zuwa Abuja, sannan ta yi jajen zan tafi na barta. Ni kuma nace Allah ya bata miji ma'aikaci a garin Abuja sai tazo can mu had'e tace Ameen. Assadiq ya Turamin kudi saboda siyan wasu abubuwan sannan yace Adda Fati ko Adda Rukayya cikin su wata ta shirya muje su ga inda muke ko Saboda gaba. Amma na fara gayamawa, Tunda ita na fara gayama zencen komawata Abuja, ita tace na gaya musu cikin su wacce ke da Sarari sai ta rakani ammh tace a madadinta Inna Talatu ta bi ni itama ta saka albarka. Haka ko akayi, Adda Fati taso taje ammh Adda Rukayya na ji tace ita zataje sai ta bar mata. Inna talatu kuma da kaina naje na gayamata tace ta na ta fama da kafa sai dai daga baya zata zo taga inda na koma sai kawai nace Ramatu da Habiba su shirya mu tafi tare. Mijin Adda Rukayya da tace masa zata rakani Abuja mamaki ya rika yi. Har yana kara tambayan kuma muna zaune lafiya da mijina ba abunda ya same sa? Adda Rukayya tace ba gashi har zan koma Abuja inda ya ke aiki ba, kuma ita da kanta da tazo gidana ta ke fad'amin. Ni sai ya ma ba ni dariya, ni kaina nasan mutane da dama suna can suna shan mamakin jina shuru a gidan aurena a karon da aka Fidda min rai a kan zaman aure. Adda Fati na ba ma kudi ta siyamin su kuka kubewa, Daddawa, Kuli yaji kayam kamshi sannan na saka aka dakamin garin kunin Alkalama na ke dama su Asim da ni kaina. Sannan har Fulawa sai da na siya, saboda Dankwake da kayan miya Bushasshe da Tumatur na dai siya duk abunda nasan zan iya nemansa acan. Kuma daman yace kayan wasan mu kadai zan dauka, ni da Zariya ba yanzu ba in ma munzo sai dai katsina Bikin Tahir sai in kuma wani abu ya faru mara dad'i wanda ba'a fata. Kayan gyaran jiki kuma na siya wajen Surayya ta aikomin da shi har da Dahuwar kazar Uwayen gida tare da Tsumi da maganin sanyi. Ni bana wasa da shan maganin Sanyi,ta dalilina na had'a ta da mutane sosai ciki harda yayyen mijina. Adda Rukayya ma na yi mata Ciniki kuma itama Saboda ingancin mganinta yasa ta kawo mata Mutane sosai. Sati biyu na yi Assadiq yazo Ranar jumma'a ya kwana Asabar muka dauki hanyar Abuja Duk wani abun da zai lalace Adda Fati na ba mawa da sauram kayan abincin mu. Maman suhailat harda hawayenta ammh tace tana shiga Abuja zata nemeni. Ni dai nace su yafemini in na yi musu ba daidai ba  Ummi tace Babu abunda na yi musu Allah ya yafe mana gabadaya. Nima nace na yafe musu duniya da lahira, har makota ma da muke huldar arziki. Sannan har makarantar da nayi Tp sun so su rikeni na musu koyarwa su rika Biyana lokacin ma zamu tafi gusau to bayan na dawo ma sai da suka kirani nace musu zan koma Abuja da zama ne. Da wuri muka fita shiyasa muka isa da wuri, ni ce a gaba tare da Asim sai Adda Rukayya da Habiba da Ramatu a baya tare da ya'yansu da Asif. Gidajen suna nan a kusa da ma'aikansu a 24 Aminu Crescent Abuja. Kuma 3bedroom ne da Falo guda biyu sai kitchen sai Tiolet a kowani dakuna sai Kuma haraban wajen ijiye mota. Kowani gida da nashi Aparment din daidai kowa bazai shiga Hurumin kowa ba. Kuma duka duka Gidaje Goma ne a waje d'aya a jere  acan kuma gefen shima goma can gaba Wajen dai gidaje talatin ne. Muna sauka shi ya fita ya barmu muna gyare gyare Adda Rukayya da Ramatu nata santin gidan komai Sabo. A albashin mutum za'a cire  har kud'in Furnitures. Sai yamma ya dawo ya kawo mana abincin da ya yi mana Takaway. Lokacin mun gama gyara gidan Tunda har mopper mun zo da shi na Zab'i dakina da na Assadiq. Shima na kawo masa wasu kayansa , kuma yace zai kwaso sauran kayansa a inda ya ke zaune. Kwana daya su Adda Suka yi min suka koma Zariya Habiba kuma Saboda makaranta, Da zai fita Office ya Daukesu zuwa Tasha ya saka su a motar Zariya bayan ya ba su Cikakken kudin mota. Ni kuma ranar ni kadai na yini dagani sai yara kamar mayya, ban fara girki ba tunda ba kayan abinci da rana da ya fita lunch ya je ya yi min Takeway ya kawomin. Da daddare ma haka, washegari kuma sai da ya dawo aiki muka fita kasuwa muka yi siyayyan kayan abinci sannan bayan mun dawo gida ya koma yaje ya kwaso kayansa a inda ya ke zaune. Tare dashi muka jera komai a muhallinsa, Shi wannan gidan akwai kayan kallo har da Firiza da A.c komai lafiya lau. Ana ta kirana ana yi min Fatan alheri. Umma da Mama duk sun kirani, Kaf yayayen Assadiq sun kirani illah ban da Salima da Sadiya da Sajida. Bansani ba ko shi sun kirashi, ni dai ban matsa kaina ba, ballatan nace masa basu kirani ba. Muka fara shimfid'a kyakyawan Sabuwar Rayuwa tare da Assadiq da ya'yana. Mu kad'ai muka fara tarewa a Estate din nan , kullum in Assadiq ya fita ya barni dagani sai ya'yana muyi ta burumtu a cikin gidan. Ba bu abunda na nema na rasa sannan ga wayata ina waya da yan'uwana tare da yan'uwan mijina. Ni kaina in na juya naga yadda Allah ya maida Rayuwata sai na daga hannuwa sama na yi ma Allah kirari da Hamdala Sannan nace"Alhamdulillah." *Janafty* *TMWB3K017* *TMW is a paid Novel, Pay 500 for regular or VIP N1K, Via 0552179550 Jamila Umar Gt bank, 09069067488* https://chat.whatsapp.com/BARBh2begGc0KdlLEZDzhk Ku zo ku yi sayayya tare da Yar Gidan Imam cikin aminci da kwanciyar hankali komai akwai harda kayan gyaran jiki hamshakan mata na supliments kala kala wanda ba su da illa, akwai kuma gagarumin haɗin mu na Arabian sabaya powder wanda babu kamarsa wannan ba irin sabayar da ki ka saba gani bace, kayan kicin dogayen riguna kuwa ba'a magana ke dai ki yi sauri ki shigo domin kwasar roman wadannan kayan. Sultana dai ta gama makircinta da kokenta kokenta na kada Assadiq ya tafi dani Abuja hak'anta  bai cin ma Ruwa ba. Na dauka daga wannan Lokacin ta Saduda ashe ba haka ba ne, ta fito da wani Sabon Tsirfa ko nace tsohon ya yi da ba wanda bai san irin wannan abun na masu kishi ba. Addabarmu ta fara yi sai muna cikin barci ance dare mahutane ga bawa ammh ita a wajenta bamu isa mu huta ba. Karfe biyu na dare uku haka zata rika Kiran Assadiq kullum kuma mganarta daya ne, abunda ke cikinta sun hanata sukuni sun hanata barci. Ko tace ta kasa tafiya maranta na Ciwo, karya dai da makirci iri iri sai kuma ta kira ta na kuka. Kuma abunda ya bani mamaki tana wajen Umma ne ammh ba ta rabo da korafin wani abu na Damunta. In yace aje asibiti sai tace ba na asibiti ba ne, da farko ya fara Biye mata sai da ya kira Umma ya gayamata ita ta yi masa fad'a tace ya fita Batun Sultana sakarci ne ita bata taba sanin wani abu na Damunta ba, balle kuma har tace Cikin jikinta ya hanata barci sai kace ya yi watanin haihuwarsa. Ashe bayan Umma tayi mgana da Assadiq sai da ta sameta har daki ta yi mata fad'a akan abunda take yi. Shikenan Sultana ta saka kuka tana fadin ita ba'a son abunda ke damunta ba kuma anzo ana cewa karya ta ke yi. Nima ranar ina zaune kusa da Assadiq Umma ta kirasa na so na tashi ya hanani, anan naji yadda Umman suka yi da sultanan a raina sai da na yi Dariya ita abun nata harda yarinyata ko rashin Hankali ne bansani ba ta na wani abu kamar wata yar fari. Duk karshen wata ya ke zuwa Gusau in ya tashi dawowa Umma ta bashi abubuwa na amfanin girki tace a kawomin wanda dai tasan zai zama wahala in aka tashi nemansa anan. Kuma ko da ya ke kokarin zuwa Duk karshen wata ya yi mata kwana uku bata gani, ita tunaninta na ba ta na fita Samun jin dadin Rayuwa. Sannan Assadiq ya fi sona a kanta kuma ta na Tutuyar Ita a Budurwa ya aureta ni kuma ina bazawara ban Canchanci samun wannan soyayyar Daga wajensa ba. Ko da yaushe ya tafi ya dawo cikin Damuwa ya ke da bacin rai duk da bashi ya ke fad'amin ba ni nake Fahimtar sanin ba wanda zai  bat'a masa rai bayan ita. Ya aureta domin Cika Umarnin da Biyayyan iyayensa ammh daidai da Rana d'aya bata bari ya Huta ba. Muna da wata uku a Abuja ta samu Hutun makaranta Lokacin cikinta ya girma watansa na bakwai. Karshen watan da yazo tace sai ta Biyosa tazo taga waje, Alhalin ko cikin yan'uwansa Anty Surayya ce kawai da Anty Sa'ima suka zo suma wani Biki ya kawosu a kuma ranar suka koma. Sai Anty Subai ita kuma bikin Dangin mijinta suka zo, itama waje kawai tazo ta gani sai su Asim bata kwana ba. Ai ko sun sha Rigima domin kai Tsaye yace mata bazata bishi ba, da ta kara sakaa masa kuka ya kira Umma ya gayamata yana ikirarin gaskiya ya gaji da Halin sultana. Umma kuma ta zo har gidan taci Mutumcinta ta kuma ce ba inda zataje ita bata duba yadda cikinta ya yi nauyi ba, sai Zalama da kishi ne a gabanta ba Fatan Allah ya Sauketa lafiya ba. Umma ta Rusa mata Tunaninta na zuwa Abuja taga a inda na ke zaune, ammh taji alwalashin in ta haihu sai taje sai dai ayi wacce za'a yi. Ni bansan cewa ma ta kusa haihuwa ba sai watan gaba da zai je na biyosa saboda Umma su ga yara, ni kuma na Duba Innani da jiki ya kara rikicewa ga ido ya tashi yanzu ko gani ma batayi ga gilashin ammh ya daina mata amfani. Assadiq da Abba sun yi sun yi ta bari a koma Asibiti Innani tace ba inda zataje a jagwalgwalata gwara su kyaleta har ta Allah ta zo ta Dauketa. Yanzu Innani tafi karfin Farida ta kula da ita Umma da Mama ke kokari suma kowacce Lokaci bayan Lokaci ta kan leka taga abunda zata taimakama Innanin da shi Tunda ko da Sandar tafiyar ma sai an kamata. Ga kuma laluran ido mai sa mai rai ya Mutu yana Tsaye. Ni na matsama Assadiq ya Taho damu tunda kadaici duk ya isheni in ya tafi aiki dagani sai su Asim,su kuma tunda suka fara tafiya suka zama mab'arnata nata, yini na ke yi fama da su. Ko Umma bata san tare zamu zo ba sai dai suka ganmu kwatsam aiko gida ya Dau murna ga su Asim ga su Asim. Shashen Umma na sauka kamar yadda na Saba, ammh sai ta saka Farida ta kwashi kayanmu ta maida bangaren Assadiq. Umma tace Abba ya ba da Umarnin indai nazo nayi masauki a bangaren mijina. Sultana na gidan sanda muka Iso Tunda ta ganni shikenan Annurinta ya Dauke kallo nan dagani har ya'yana da kowa ke santin su ganin sun Fara tafiya bamu isheta ba. Nima ko wannan karon naji mganar Assadiq da yace in bata girmamani ta gaisheni ba nima bai kamata na zubar da nawa girman na bita ina gaisheta tana min wulakanci ba. Na ganta ta kara ramewa ko ni da Cikina na fita kyen gani ta yi baki sai kuraje sai dai haka ta rika Turamin ciki gaba tana wani tale kafa ko an gayamata ban ga cikin ba ne Oho? Siyama na gidan muka iso ita naji tana yi mata kirari da Maman Biyu. Sai bayan mangariba Assadiq ya kwasheta zuwa gidansu. Shashen Innani naje gaisheta na iske ta sha magani har ta kwanta daganan sai na koma Shashen Mama itama na iske bata nan suna bangaren Abba ita da Umma tare da Asim. Sai Siyama kad'ai na gani da tace min itama yanzu megidanta zai zo ya Dauketa. To da yake ta na kirana a waya kuma sannan mu kan yi yar Hira a chart,sai na zauna muna hiran inda muka koma ina gayamata zaman bariki ba dad'i yanzu haka wajen mu Biyar ne a Estate din mu, mu biyu ne musulmai Kafayat bayarbiya ce itama. Saurn  duk ba addinimmu d'aya ba, ni da ya ke ba na fita ba ganinsu na ke yi ba kafayat ne ta shigo waje na sau daya muka gaisa nima na shiga wajenta sau daya. Ita tana sona saboda su Asim sauran kuma sai dai daga nesa a daga ma juna Hannu ina gayamata na zama kamar mayya ni kadai a gida sai yara in Assadiq ya fita Office. A bakinta nake jin Diraman Sultana kwanaki na sai ta bi Assadiq a Abuja sannan take gayamin ta gama yad'a cewa itama yan Biyu zata haifa. Ina dariya nace"Allah ya ba ta." Siyama tace"Tab Anty Siya wannan cikin na sultana bani da sanin gaibu ammh ina da tabbacin Daya ne aciki." Ni dai ban ce komai ba sai dai na yi mirmishi. Ban tambayeta ba ta fara fad'amin daman su Anty Sajida ke zugata kuma shiganta makaranta ta yi Sabbin kawaye suna Hore mata kunni. Ni dai bakina kanin kafatana Allah ya kyauta kawai nace sai dai abun da ya bani mamaki da tace min har ita Sultana ta janye mata tunda ta samu masu bata Shawaran da ta ke so. Ko kuma tana ganin tunda ita bata shiga jami'a ba yanzu ta wuce da saninta ni kuma sai na tambayeta me yasa bata Cigaba da karatu ba?. Kai Tsaye tace mijinta yace ba yanzu ba. Ni fa duk wani abunda Sultana ke yi ba na sani sai na had'u da yan'uwan Assadiq, tunda shi dai baya gayamin aiko zuwana naji mganganu kala kala na mganar kayan haihuwa tace ma Anty Surayya wanda zata siya mata yafi nawa Tsada sannan kuma ita yan Biyu zata haifa duka maza Saboda haka kayan jarirai na Guda biyu za'a siya. Da Surayya tace mata a takardan Scan ance yan Biyu ne? Shikenan tace wai ta karyata ta, tunda Sultana ta fara zuwa awo kuma ba wanda ya taba ma ganin Takardan Scan din nata waya sani ko Assadiq din ya gani. Karshe dai Anty Surayya ta tattara kudin siyayya ta mikama Sultana tace ta siya da kanta shine Ta kira Sajida suka shiga kasuwa tare suka siyo abunda suke so. Da Assadiq yaji yace a kyaleta tayi duk abunda taga yafi yi mata daidai. Anty Surayya ta ke gayamin da ta zo gidan muka shige shashen Assadiq in da na sauka muna mgana. Da yake akwai shakuwa sosai Tsakanina da Surayya muna hiran da ya shafe su sosai tace ai yanzu na Riga na zama SS Shinkafi. Kwana uku muka yi ranar Litini da Safe muka koma Abuja, sai kuma Bikin Tahir da shima saura wata Biyu har Abuja yazo ya ga inda muke. Tunda Taron siyasa ya shigo da shi garin Ranar har wajen 12 na dare suna falo da Assadiq suna hiran su. Yanzu Tsakanina da Tahir sai gaisuwan mutumci da girmamawa. Mutanen Zariya kuma sai dai mu yi magana ta waya. Hankalin Amma a kwance tunda ta na da tabbacin ina zaune lafiya da mijina tare da kyakyawan Rayuwa ni da ya'yana. Bikin Tahir ya matso kuma Assadiq ya gayamin kila Sultana sai ta haihu kafin a yi bikin Tahir, ni kuma a raina sai nake fatan Sultana ta riga haihuwa in muka tafi gusau daga can muka tafi katsina Biki. Tunda Ankon bikin ma ta hannun Amaryan Assadiq ya siyamin, Tahir ya bata lambata ta kirani na fad'a mata masearuement dina. Shikenan sai muka fara gaisawa ta Chart, ta na tambayansu Asim tunda tace Tahir na Tura mata Hotonansu. Hauwa'u Amarya ta gayama Angonta Katsina zan zo wajenta Biki, sai dai na bari in za'a kawota Daura na Biyota tunda anan babban gidansu za'a yi walima sai ta kwana Biyu sannan Mijinta ya dauketa su koma Katsina. Assadiq yazo yana gayamin nace masa shikenan nima tamin mgamar nace sai abunda Mijin Siya yace. Shi kuma yace mijin siya ya ba ta dama ta fara sauka katsina a sha Biki lafiya. Ana saura Sati Biyu Bikin Tahir Sultana ta Sauka an samu mace, na ci Dariya Sanda Siyama ta kirani ta bani Labarin abunda ya faru a asibiti Lokacin da Sultana za ta haihu. Tun naguda bata kankama ba ta kwanta ta na Raki Umma da Mama suka kwasheta sai asibiti. Suna zuwa ta rika ce ma likita ita yan Biyu ne acikinta bazata iya haihuwa da kanta ba sai an yi mata C.S. Likita ya fito yana gayama su Umma su Daya suka gani acikinta. Sannan Mahaifarta ma bata Bud'e ba kuma zata iya haihuwa da kanta ammh tana fadin ayi mata aiki yan Biyu zata haifa. Kuma Nurses sun sha Fama da ita a dakin haihuwa ta ki bude kafa ballatana su yi aikinsu ai ta dauka Haihuwan wasa ne sai da ta ganta zahiran ta gane bata da wayau bakinta ya Mutu. Tana gayamin Umma na ta fad'a tana fad'in bata tab'a sanin sultana mahaukaciya ba ce sai ranar, Ita a tunaninta C.S din wani kayan gabas ne, ko kuma Haihuwan wani cin Tuwo ne ai da ta haihuwa sai bakinta ya yi murus sai ido ga shi ta karu ta sha Dinkin adadin kuka da Ihun da Sultana ta yi bai da iyaka. Assadiq ko ya sha Allah ya isa yafi cikin kwando. Tun ballatana da ta farka taga bai zo ba harda kukanta da ya kirata ta fara mai korafin bai zo ya ganta ba Alhalin ya gama kunsa mata wahala ta kusa mutuwa. Ammh nan da matarsa zata Haihu bashi da ko lafiya a haka yaje ya ganta, ita ko tunda bata da matsayi bai zo ya ganta ba ballatana yaga abunda ta haifa. Shi dai hakuri ya bata Tunda Talata ne ta Haihu da safe kuma ranar aiki ne shiyasa yace sai Ranar jumma'a zai taho gabadaya tare da Siya. Sannan can gida ne kowa na tare da ita kuma suna waya da Umma yana jin Halin da ake ciki a ganinsa zuwansa kuma sai ya ke ganin kamar raina kokarin Su Umma ne. Ita ko daman ga rashin haihuwan yan Biyu sannan ga shi ta Haifi mace gani ta ke yi kamar Darajanta ya sauka. Hasiya tafi ta har yanzu, kiri kiri taki bama yarinyar Nono wai zafi take ji sai da Umma ta fita yamma da Hankalinta sannan ta fara bata Nono ta na yi ta na kuka. Kwanan su Biyu a asibiti aka sallamota zuwa gida Bangaren Umma ne tunda itace uwa Dakin ta na baya tun na yanmatanci nan aka gyara mata zata yi zaman jego. Ko'ina kuma an sanar da Haihuwarta Mutanen shinkafi dai nata mamaki jin ance mace ta haifa kuma ba yan Biyu ba. Da kuma an ce Sultana ya muka ga D'aya ba Biyu ba? Sai ta fashe da kuka kamar wacce aka yi ma duka. Tunda kuma ta haihu ta yi ta Turen turen baki ita a dole Assadiq bai Dauketa da Muhimmanci ba. Ta yi ta kiranshi tana yi masa korafi shi wlh har fama ya ke yi da Fad'uwan gaba in yaga kiran Sultana saboda yasan matsalace da korafi da ba'a yi mata daidai ba. Tun kafin mu taho na saka Siyama ta turamin Lambarta na kirata domin na yi mata barka. Inaga ta gane muryata ne cikin Gadara tace"Wa ke mgana? Ni kuma kai Tsaye nace  mata"Hasiya ce an sauka lafiya? Kawai sai ta yi tsaki ta kashe wayar na yi ta mamaki daga aabun arziki. Daganan ban kara kiranta ba sai itace ta kara kirana na dauka ma bata ganeni ba ne daga farko. Ina dauka ta fara fad'amin mganganun banza wai na hana Assadiq zuwa ya gansu to na sani ban isa na shiga tsskaninta da Mijinta ba. Har zagina ta yi tana kirana Annoba kuma bazawara. Ni na gaji da jinta na kashe wayata ta yi ta kira ban dauka ba sai Sako ta Test massages har da wai kada na yi tunanin na haifi maza na cinye gida itama zata haifi nata na zura ido na yi kallo. Abun nata ma sai ya koma min kamar bata da Tunani yarinyar nan gaskiyar Umma ne mahaukaciya ce. Ko Assadiq ban gayama ba, na dai ce masa na kira sultana na yi mata barka kuma naga yaji dadin haka. Su Umma daman tun ranar da aka yi haihuwan na kira su na yi musu barka hadda Abba. Shirin gabadaya ni na yi tare da yara Tunda daganan katsina zan wuce bikin Tahir shi kuma zai dawo Abuja daga Abuja zai zo katsina Saboda ya Samu Daurin aure. Ranar jumma'a da yamma muka iso Gusau. Yara tun a haraban gidan muka Rabu da su to ya'yan dangi ne fa Tare da Assadiq muka fara shiga wajen Abba muka gaisa sai Bangaren Innani. Allah sarki yau jikin da dana ma, ta na kwance sai dai bakin ne yau ya Bude har suka yi ta hira da magajin gida. Ni nan na barshi na tafi zuwa bangaren Umma kayanmu kuma an shiga da su shashen Assadiq. Ko da na shiga shashen Umma cike da baki masu barka. Anan naga su Anty Sakeena ita kadai ta tarbeni, Sai Umma da tun a haraba muka had'u muka gaisa. Dakin mejego kuma cike da kawayemta yan makaranta da su Sajida da Sadiya. Sakeena ta rakani na shiga domin na yi mata barka ammh ina gaishe su ba wacce ta amsa sai kallon banza. Itama Sultanan kai ta kauda ta na mgana da wata a kusa da ita. Ni dai naga suna nuna ni suna Dariya suna kuskus kasa kasa. Sakeena ce ta kalli Sultana kafin tace"Sultana baki ji Hasiya na miki barka da sauka ba ne? Baki ta tabe kafin tace"Ban ji ba yauwa.! Daga haka ta cigaba da mganarta ina Tsaye ina yake sakeena ta isa kusa da Sajida ta na fadin"Sajida bani jaririyar Hasiya ta ganta." Kamar ta watsa mata kankara haka ta mike a firgice ta na fad'in"Wata jaririyar? Wannan? Ta fad'a ta na nuna jaririyar da ke cikin kayan sanyi a gefen uwarta. Sultana ta yi caraf ta dauke yarta ta na Fadin"A'a kada a goga ma yata Mugun Jini." Sadiya ta karbe da fadin"Wlh kuwa gwara ki yi can haka da ita, kada yanzu kajin Tsiya da bala'i su fara Bibiyanta" Gabadaya sai naji na muzanta idanuwana suka tara kwallah ammh sai na Shanye. Sakeena ce tace"Haba don Allah, daga abun arziki kuma miye ya kawo wannan mganar? Sajida tace"Wani abun arziki waya san abunda ta kunso a hannunta tunda ba Allah a ranta? Kawai ta Dauki yarinya ta goga mata wani abun tsiya, tunda ita dai Bakar Annoba ce Tsiya tsiya jinin bala'i da Farar kafa. Tsiya nan ta ganta ta barta ke ai ganin ki bala'i ne da masifa in da kuma kika shiga kika zauna shima bala'in ki zai iya fad'ama waje, gwara ki koma inda kika fito barka ne ko? To mungode Allah ya ba da lada ammh a kara gaba, ban da munafunci miye na Biyo miji barkan kishiya? Zugwai zugwai ko kunya baki ji ba." Ta ke fad'a ta na nuna min hanyar  fita, kaina na kasa ina kokarin yaki da kaina ba na so na yi kuka su gani sai kawai na yi mirmishi na juya. Sakeena na bari ta na yi musu mgana sai abun ya koma kanta itama..na fita falon Umma ba na gani Saboda Duhu ya mamaye ganina da kuka da ya taso min hawaye sun fara zubarmin. Na ci karo da Sa'ima ma ban sani ba tana min mgana ban Tsaya ba, da gudu na tafi bangarena ina kuka. Bansan cewa fad'a ya hautsine tsakanin Sakeena da Sajida ba Sai da Anty sa'ima ta shiga tsakaninsu. Kuma a gaban kawayen sultana to ai suma su san komai tunda ta gayamusu komai. Mgana ta kai kunnen Umma da Abba har da Assadiq da baya nan yaje gida ya yi wanka. Anty Surayya ta kirasa tace itama Sa'im ta kirata ta na fad'a mata Sajida ta zazzagi Hasiya. Ya zo gida nan ransa a bace ya so ya ga Sajida ta raina kanta sai kuma ya yi rashin sa'a Abba ya yi ma ta fata fata shima yace in dai ba alheri ke kawo ta ba  kada ta kara zuwa..nima yazo yaga na warware tunda Umma ta bi ni ta yi ta bani hakuri har da Abba ma nace musu komai ya wuce. Fadan Assadiq a kan Sultana ya sauke ya yi mata Tas yace kuma ba Hasiya ta Tozarta ba shi ta tozarta kuma ya gode ta yi duk abunda zata yi lokacinta ya kusa karewa. Haka ta dinga kuka tana fadin na yi mata sharri, ita ko baki bata saka ba sannan itace fa ta haihu duk wahalan da ta sha bai Tausayamata ba sai kawai ya kamata da fad'a. Abunda su ka yi min ko kadan ban sakashi a raina ba tunda ai ba wannan ne na farko abunda na gani ba. Tozarci ba irin wanda ban gani ba, Shiyasa na maida komai ba komai ba tare dani ake yi ma sultana Hidima. Yarinya taci sunan Umma Wato Salamatu. Anyi taron suna Ranar talata ammh bai yi wani armashi ba. Maijego fuska ta kumbura da kuka Saboda angon karnin yaki siya mata Zinare. A bakin su Sakeena na rika jin mganar ranar suna, ni kaina da ba Assadiq ba na fara gajiya da Sultana daga wannan sai wannan. Wai kuma wani iskanci da ta dauko D'an kunnen zinare zai si ya mata taci suna da shi a matsayin Kyautar Haihuwan da ta yi masa. Shi kuma yace ba shi da kudi akwai bikin Tahir sannan zirga zirgan kai da kawo mai na cinye masa kudi ya kawo mata mganar hidima ta yi masa yawa ga nawa da na yara sannan shi ya ke rike da Hidimar Innani. Saboda dai shima yau ace yana da amfani a gidan su. Ammh Sultana taki jin Lallashi tace sai ya siya mata shi kuma yace bazai siya mata ba. Shikenan ta ke kuka Ranar sunan yarta ta yini ba walwala. Ni abunda ke bani mamaki gasa take yi dani, taga zoben zinare a hannuna ni kuma Kud'aden da na samu da haihuwan yan Biyu ne da kuma kudin da na ke tarawa a hannuna. Karami ne ma na dubu 230k na siya Adda Rukayya ta bani shawaran na siya saboda kaddara kuma da na bar kudin duk sai na kashe su, sannan kuma ban siya ba sai da na Nemi izinin Assadiq yace yana da kyau hakan. Nasan kuma ita tunaninta Wlh Assadiq ya siyamin shine zata saka Rigiman itama sai an siya mata. Kai jama'a ni ban taba ganin kishi irin na Sultana ba. Ka yi da kishiya kuma ka yi da miji Saboda sakarci. Ni sai na rika Allah Allah ma na tafi katsina Biki duk sai gidan ya isheni, yarinyar nan tsirfarta ta yi yawa. Sajida kuma ko suna bata zo ba taji Haushin mganar da Abba ya yi mata. Sadiya dai tazo ta na ta harare harare da jefa manganganu. Yara kuma sai dare na ke ganinsu suna wajen Umma ko mama, in Abba ya dawo gida suna tare da shi. In kuma suka ga Babansu su manne masa tunda yanzu su san kowa. An yi suna Talata, Jumma'a muka tafi katsina tare da Assadiq tun da bai koma ba. A gidan Amarya Hauwa'u na sauka Tahir ma na garin shi yaje ya tarbemu, ni kaina naga tarba Hauwa'u kamar ta taba ganina. Ko'ina sai ta nuna ni tace matar Abokin Tahir ne Sadiq. Su Mama sun ce sai dai mu had'u a Daura har da su Anty Surayya duk za su je ma Hajja Biki Sanadin Tahir. Abba ma yace zai zo daurin aure sannan 100k ya tura ma Tahir Gudummuwa. Ranar asabar aka Daura Tahir da Amaryansa Hauwa kuma a ranar suka kwashemu zuwa Daura. Ankon less ne ya yi das a jikina kamar an auna ni, gwamin ban sha'awa tunda ban wasa da kunin sabaya. Saboda ni dai ina so na ganni da jiki ba na son ramar nan nawa. Sai kananun halittun jikina su rika bayyana. Mutane ma kallon mai ciki suke yi min, Har Anty Surayya sai da tace ko Ciki gareni nace tukunnah dai Kuma ban saka tsarin iyali ba Tazara ne Allah ya bani, ina fatan sai su Asim sun shekara uku ko da zan samu wani cikin. Tare muke da Matar Abokinsu Mb, Jb dai bai yi aure ba, bai gama iskancin na shi ba. Motar Mijina na shiga zuwa Daura tunda suma su Mb kowannen da Motarsa sauran motocin kuma suka kwashi Amarya da Ahalinta. Acan daura muka hade da Mama da Anty Surayya sai shahida da A gusau taje barkan Sultana daganan ta Biyo su Mama daga kuna nan zata koma katsina. Hajja da yan'uwan Tahir sun yi ta godiya wannan karan sosai Umma ta ba da kudi da kayan abinci an kawo ma Hajja. Kwana daya muka yi a Daura muka wuce Abuja ni da Assadiq da yara, wasu kayanmu ma na gusau yace na bari karshen wata in ya koma sai ya Taho mana da shi. Sallama sai dai ta waya su Anty Surayya daman mun riga su tafiya, yace in ya tafi ya barni wahala ne kuma sai an saka wani ya maidani gida. A daura muka bar Amarya Hauwa'u da Angon Tahir, sai fatan Allah ya ba au zaman lafiya. Mun koma Abuja bamu san abunda ya faru a gusau ba. Ashe a satin  da aka yi Bikin Tahir Mijin Sajida ya dankara mata saki har Biyu. Rigima ta yi da Danginsa kaca kaca shi kuma ya saketa. Sakin aure bai da dadi, kuma ba wanda ya kirani ya fad'amin Anty Surayya ce kuma kwana Biyu bamu yi mgana ba. Siyama kuma bamu yi waya da ita ba. Kuma Assadiq baya gayamin irin wad'anan abubuwan. Nima sai da naji suna mgana da Anty Surayya. Yana cewa"Allah ya kara mata, ba tun yau ba nasan abunda Sajida ta shuka watarana shi zata girba." Sai da suka gama wayar ne na tambayesa abunsa ya faru. Shine ya kalleni kai Tsaye yace"Sajida ce mijinta ya saketa saki biyu, Abba ya kirshi sun zauna mganganu ba dad'i ashe acan dangin nasa ma munafunci da Rigime rigime ta ke ta had'awa dara taci gida mahaifiyarsa tace ya saketa." Cikin jimami nace"Innalillahi Abu bai yi dadi ba" Mikewa ya yi lokaci d'aya yana fad'in"Ya yi dad'i mana, ai kad'an ta gani wanda yace daman tukunyar wani bazata tafasa ba ai tashi ko Dumi bazata yi ba." Ni dai ban ce komai ba, har ga Allah jikina ya yi sanyi. Saki ai ba shi da dad'i, ina ga shiyasa ba wanda ya kirani ya gayamin Labarin ba dadi. Anty Surayya kuma ke kiranshi inaga kan mganar har cewa ta yi yaje Gusau yace ba inda za shi shi yana da abun yi. Umma ina ji ta na kiranshi, kan mganar sai ya zille mata da mganar aiki daga karshe dai ba'a samu masalaha ba, mijin Sajida ya zuciya ya kuma ce har Abada duk da ya'yan da ke tsakaninsu. Dole kanwar naki ta dawo gida ta fara Idda, ga ta  ga Sultanan sai su cigaba da munafuncin na su. Su dasa daga inda suka Tsaya in ji Surayya. Take gayamin da muka yi waya da ita, a bakinta naji ba'a daidaita ba, Sajida na gida. *Janafty* *TMWB3K018* *TMW is a paid Novel, Pay 500 for regular or VIP N1K, Via 0552179550 Jamila Umar Gt bank, 09069067488* https://chat.whatsapp.com/I7uxPXgtPKBHnVQjaEbRlE *LAME NIG!* *KASAITATTUN MATA MUN GAISHE KU*. *AISHA LAME TA KAWO MUKU DUKKAN NAU'IN KAYAN KWALLIYA*. *KUNSAN GWANAACE WAJEN BAWA FATA HAKKIN TA* *KUN TUNA KYUAN FATAR GUDUYO KO?* *KUN TUNA DAI YADDA BULKACHUWA KE SIYAWA YABI KAYAN KWALLIYA NA ORIFLAME KO?* *TO KEMA GARZAYO KI ZABI NA KI, KO TA ZABA MIKI WANDA ZAI FI DACEWA DA FATARKI*. *BA IYA KAYAN ORIFLAME BA KAD'AI.* *TANA DA PRODUCTS DABAN DABAN MASU KYAU, MASU MASTAKAITAN FARASHI*. *KU TUNTUBE JIKAR DADAR MARINA A WANNAN LAMBAR 07036662633*. *ADO DA KAMSHI NE SIRRIN GAYU* Daga Sajida har su Umma ba su tab'a Tunanin Sajida zata iya tsintar kanta a cikin zawarcin da ta samu kanta a ciki Dumu dumu ba. Sajida ta gama sakankancewa da ta kama gida ta kuma fi karfin wani ya tugeta, ta na ganin Yusuf mai Hakuri ne sannan mai kawaici wanda baya maida kai kan wasu abubuwa kuma ta na ganin cewa ta Haihu ga ya'ya uku a tsakaninsu tana ganin babu wanda ya isa ya iya ja da ita. Ta saki jiki ta na ta rashin mutumcin da ta saba daman tun tana gidan Sajida akwai munafunci sannan in dai ta zauna a wuri ba ta yad'a alheri, kuma bata sulhu sai dai ta kara Hura wuta. Bayan ta yi aure ma bata daina ba, a makota ne a dangin mijinta ne duk inda ta shiga ta zauna bata yad'a alheri ba sai dai ta fad'i sharri ta Hura wutar wata fitanar. Bata kuma shiri da wasu kannen mijin nata tun tuni shima mijin nata ya sha ja mata a kunni karya ne su had'u a taro Sajida ba ta watse taron nan da fad'a ba, ita kanta mahaifiyarsa bata son Sajida sabida tace ba mutuniyar kwarai ba ce. Bata son zaman lafiya, Ta dad'e ta na yin abubuwa Yusuf din da kauda kai sai wannan na karshenta da wa'adin auran na su ya kare. A gidan sunan matar kanin Yusuf din, Ta yi fad'a da kannensa har suna zaginta ita kuma tace sun san wacce suka zaga wannan Tsohuwar mai Dattin dankwali na gida. Ai ko ba sanya suna zuwa gida suka gayama Mahaifiyarsu ga abunda ya faru har suna kari, nan ta ke ta kira Yusuf tace ya sauwake Sajida kila in ta d'andani zawarci zata yi hankali. Shine dalilin da yasa ya saketa sannan Saboda a kara kuntata mata uwar tace duk ya kwaso mata yaran ya kawo mata hadda wanda ta yaye. Zaman da Abba ya yi da shi sai ya Fahimci Sajida ta canchanci ta zauna a gida ta ga rayuwa kila ko zata yi Hankali shiyasa shima bai kara neman Yusuf ba. Ballatana Assadiq da yace Allah ya kara gwara da ya saketa kila nan gaba zata Fahimci rayuwa ko Allah zai saka ta zauna lafiya da kowa. Ita ko Sajida da farko ta dauka wasa ne, Ta na ganin Yusuf bazai iya Rabuwa da ita ba wasa ya ke yi, zai zo da kafarsa ya neme ta ya kuma bata Hakuri ya maidata gidansa. Shiyasa ko da ta dawo gida da Abba ma ya kirashi Haushi ta rika ji a tunaninta za'a zubar mata da Ajinta, sai da taga har ta shafe wata d'aya a gida har jini daya ta yi ba Yusuf ba sakonsa sannan ba wayarsa. Daman tun faruwan abun bata kirasa ba ta zauna ne sai ya nemeta da kansa sai ta fara ganin karshenta. Umma ta damu da wannan Lamarin sannan nadama ya shigeta, In ta zaunar da Sajida ta na mata fad'a sai ta rika Tura baki tana fadin Yusuf zai zo da kafarsa har dakin Umma ya Duka ya bata hakuri. Sai da ta ga lokaci ya fara tafiya bai zo ba, sannan bai kirata ko a waya ba. Sannan ga shi ta fara gajiya da zaman gida kewar ya'yanta take ji sosai da gidanta inda ta ke yi duk abunda taga dama ba nan da ba ta da ikon yin wani abu ba. Sannan abun da ya bata mamaki yan'uwanta kowa sai yace laifinta ne, ita taja ma kanta saki kowa sai ganin laifinta ya ke yi, har Abba haka ya kirata ya yi mata kaca kaca ita kuma a ganinta bata aikata komai ba sai ma gani take yi da mutane ba sa son gsskiya ne. Yanzu haka a daki d'aya suke kwana da Sultana tunda a bangaren Umma ba wani daki sai nata, ga shi cikin Dare Mai sunam Umma da suke kira da Ummi akwai kukan dare, Sultana juyawa ta ke yi ta sha barcinta ta barta da renon yarta. In ta tasheta sai ta tashi ta na alamun barci barci in an samu ta bata Nono sai ta sakar mata yar ta koma ta kwanta tana fad'in kanta ciwo ya ke yi, sannan Umma da farko ta na shigowa ta taimaka mata itama in bata bangaren Abba to daga baya ma sai ta rika barin Sajidar da wahala ta bakinta tace tunda ta na kusa ta taya sultana jegon, kuma ma dai ai ta girmemeta a harkan ta rika nuna mata wasu abubuwan Sajida ta na shuru da farko sai da taga Sultana ta maidata kamar Nany mai renon yarta, komai na ta ba tsari ba gyara ga son jiki da kazanta komai a watse sai dai in Sajidar ne zata gyara, in kuma ta yi mata mgana sai tace"Ni fa Anty Sajida na gaji ne, da me zan ji da kula da yarinyar ko da gyaran daki da kaya? Ai Umma tace tunda kin dawo gida kina zawarci ki rika tayani kina taimakamin mana." Ranar Sajida ta sha mamaki kuma ba ta tab'a sanin haka kalmar zawarci ke da zafi ba sai da kanwar bayanta Kamar Sultana ta gasa mata mgana. Abun ya yi mata ciwo kwarai ta samu Umma ta gayamata. Umma ta yi wata dariya kai Tsaye ta kalli Sajida ta na fad'in"Ai ba karya ta yi ba, gaskiya ta fad'a tunda kin fito zawarci baki da wani amfani sai na Tayata kula da yarta, daman kuma bata da wata abokiyar shawaran da ta wuce ki ke da Sadiya, to tunda ita Sadiya na gidanta ke ce zaki zauna da ita kinga ma shikenan sai ku yi ta bama juna shawarwari ko? Sajida bata gane mgana Umma ta gasa mata ba, sai da tace"To Umma ya dace ta wani ce na dawo gida ina zawarci? Ni ai ba sa'anta ba ne, duk kokarin da na ke yi mata bata gani? Ni fa ban tab'a ganin sangantattaciyar kazamiyar mai jego irin ta ba wlh." Umma dai yar dariya ta yi a ranta kafin tace tun yanzu? Ai ta dauka da saura kafin zama yasa kowa yasan halin kowa. Kuma sannan Sultana sai ta fara yi ma Sajida wani abu sai ana zaune sai ta kalleta cikin kamar mamaki ta na fad'in"Yanzu wai da gaske shikenan Anty Sajida kin zama bazawara? Tambayar irin cikin izgili da Dariya da Renin hankali. Sannan kuma ko a gaban waye ta kan fad'i haka ko a jikinta ita a dole da sunan wasa. Tun Sajida na nuna bata jin haushi har ta fara nuna mata, sai tace ita a wasa ta ke mganarta. Sannan wani karin abun haushin ma Har makaranta in Sultana zata shiga sai Umma tace su je tare da Sajida ta rike mata Ummi in sun shiga karatu. Abun kuma da ya faru ba'a shiga da yara a ji, ita kuma Sultana tace a daukan mata mai reno. Ko kuma Anty Sajida ta rika rakata makaranta ta na rike mata Ummi, ita kuma Umma ta amince tace tunda Sajidan na gidan bata komai idda ta ke yi, kuma tunda fitan ta zama ta lalura ta rika raka Sultana cikin makaranta. Sajida bata kara jin ta raina kanta ba sai ranar da ta raka Sultana makaranta Lokacin har ta yi arba'in sai dai bata koma gidanta ba sai Assadiq ya dawo. Yafi wata bai zo ba tun tafiyarsu ta bayan suna yana ta kawo uzurin aiki ne ya rikesa. Tun safe suka zo, ita ta na waje rike da Ummi ta na fama da ita, ga sanyi Lokacin an fara iskar sanyi Sultana kuma ba su fito ba sai Wajen sha daya na safe sai gata ita da zugan kawayenta. Suna zuwa suka ga Sajida rike da Ummi, cikin kawayen nata wata ta kalli Sajida ta na fad'in"Nanny ko da kika samu mai hankali daga gani zata kula da Ummi sosai." Sultana ta kalli Sajida ta wani kyalkyace da Dariya kafin tace"Wata Nanny? Ba fa nanny ba ce Yayar mijina nace Anty Sajida da ya ke baki samu suwa suna ba ne shiyasa baki ganta ba, ammh ai su Maryam su santa." Sajida ta na ji a gabanta Yarinyar tace"Au yi hakuri, na ganta a nan ne lafiya? Sultana kai Tsaye tace"Zawarci ta ke yi mijinta ne ya saketa." Ta fad'a ko a jikinta har ta na wani Dariya wani abu ya daki zuciyar Sajida. Sai a lokacin ta kara jin girman nauyin sakin aure ga Rayuwar y'a mace, Shiyasa tundaga ranar ta fara kiran Yusuf domin ta samu ta lallashesa ko zai maida ta dakinsa. Ammh ya ce mata umarnin mahaifiyarsa sai sanda tace ko zai iya maidata kuma ma shi ya gaji da hallayanta gwara su rabu gabadaya zai fi. Hankalinta ya yi bala'in tashi tana ganin tun yanzu ta fara ganin Rayuwa kudi ma sun fara yanke mata, ta fara fuskantar rayuwar da bata santa ba. Umma ba ta bata kudi Abba kuma bata isa ta tunkare ta ba, komai nata ya kare kayan kwalliya kati ma a waya na fara gagaranta gashi ba wata sana'a ta ke yi ba, da aurenta ta ke takama ba da komai ba. Data ma yanzu ba ta dashi in kuma ta roki su Anty Surayya ta na ganin tasaukar da Ajinta Sadiya ta kan roka ta wurga mata 1gb daga baya itama sai tace ba kud'i a hannunta. Sultana kuma ko ta na dashi bazata bata ba, tunda ta taba rokonta 5k tace itama ai d'aya suke tunda Mijinta baya tare da ita yana can tare da kishiya. Kuma tasan ta na da kudi Sadiq ba mutum ne mai mugunta ba. Umma kuma bata ko bi ta kanta ta na ta yi ma Sultana Shirye shiryen komawa gidanta cikin satin nan. Ta kuma siya mata kayan gyara na abunda uwa zata yi ma yarta, daga Shinkafi ma Matan Babanta sun aiko mata da mganin sanyi da Tsumin Amare. Itama ana ta bangaren da Taimakon  Surayya ta gyara Sultanan sosai, kuma ta yi mata kyakyawan Jego mai kyau ta maida jikinta ta yi sharr  ita da Ummi. Sadiq ya yi waya da Umma zai dawo ranar jumma'a. Suna zaune a falo a daran Laraba ita da Sajida ita Sajida wayarta ke hannunta ba ko data game ta ke yi ta na rage zafi. Ummi na bayan Ummi ta goyata bayan ta gama yi mata wankan yamma sai ta samu barci. Sultana kuma tunda ta shiga ciki sallah bata fito ba. Umma ta yi zaune ta na kallon Sajida ta na kara nazarinta kamar ta na bata Tausayi ammh bata so ta nuna mata tana jin Tausayinta. Kuma har Allah ta ga abunda Mallam da Sadiq suka rika gayamata. Ba ita ke da littafin kaddara a hannunta ba  Allah ne itama ko ita kanta bata wuce zama bazawaran ba. To ga shi bai faru da ita ba ya Faru a kan yarta itama Sajida ta na daga cikin masu kyaamatar bazawara da aibata kaddaran da ba mutum ya zana ma kansa ba. Sajida duk ta rame ta yi baki kamar ba ita ba, Umma ta sauke ajiyar zuciya kafin tace"Sajida wai nace baki kira shi Yusuf din ba ne? Sajida ta kalli Umma cikin wani yanayi kafin tace"Umma ya ma daina daukan wayata yanzu, yana so na fa duk sharrin kannensa ne da uwarsa." Umma ta kalleta kai Tsaye kafin tace"Uhm ashe har yanzu da Sauran ki ban sani ba Sajida? Sajida ta tura baki kafin tace"Umma to ni me na yi? Har da ya'yana sai ya rabani da su? Sai idanuwanta suka ciko da kwallah tana kaunar ya'yanta Damuwarta akansu ma tafi yawa, tunda ta yi aure ba ta taba kawo ma kanta zata iya dawowa gida ta zauna da sunan wai mijinta ya saketa ba, hasashen da bata tab'a yin kamarsa ba. Ganin abun ta ke yi kamar a mafarki, kuma tabbacin ba mafarki ba ne. Suna nan zaune sai ga Sultana ta fito tana fad'in"Umma yaushe zan tafi Shinkafi na kai ma Baba Ummi ya ganta ne? Umma tace"Sai ki jira mijin ki ya dawo in ya barki duk sanda kika Shirya sai ki tafi." Kai Tsaye Sultana ta zauna kusa da Sajida ta na fad'in"To Umma shikenan ma sai Anty Sajida ta rakani saboda Daukan Ummi." Daga Umma har Sajida sai da suka kalli Sultana ita ko har acikin ranta ta yi mganar. Umma ta kauda kai ta na fad'in"Sai kuje tare itama ta kwana Biyu ba ta je ba" Sajida na gefe ta bi Sultana da wani kallon Lalle ma yarinyar nan.. Cikin gatsali tace"Ke ba inda zani." Sultana ta kalleta cikin mamaki tace"Saboda mene? Kawai sai Sajida ta mike a fusace ta na fad'in"Bansani ba mara kunya kawai." Ta fad'a lokaci daya ta na wucewa cikin Daki a fusace. Suka bi ta da kallo Sultana ta kalli Umma Lokaci d'aya ta na fadin"Umma me ya samu Anty Sajida kuma? Umma ta ce"Ina zan sani, me yasa baki bita kin tambayeta ba? Sultana ta tabe baki kafin tace"To ni me na yi mata da zata ce min bani da kunya? Umma na jinta ta na kunkuni bata tsnka mata ba, ta yi kamar ba ta ji ta ba. Ganin Umma ba ta bata fuska kan mganar Sajida ba yasa ta sauya Hira da fad'in"Umma zan sha yawo har Abuja zani fa." Umma ta kalleta a karkace kafin tace"Gidan wa zaki je a abuja? Kai Tsaye tace"Gidan mijina mana, kema Umma da wata mgana ina da inda zan je da ya wuce gidan Yaya Sadiq na Abuja." Umma ta gyad'a kai kafin tace"Na sha'afa ne, Allah ya kai ku lafiya." Ta amsa da Ameen sai ta fara yi ma Umma korafin Sadiq wajen wata daya da sati bai zo ya gansu ita da Ummi ba tun bayan suna da ya tafi. Cikin Kishi tace"Umma don ina adalci anan, sai kuma yazo ya yi kwana Biyu yace zai koma sai mutum ya yi mgana aga laifinsa." Umma na zaune kala bata ce mata ba har tagama mganganumta. Ummi ce ta tashi ta kuma fara kananun Rigima yasa Umma ta sauko mata yarta ta bata. Ita kuma tace bari ta shiga bangaren Innani ta dubata. Kai Tsaye Sultana tace"Allah Sarki Innani, ki gaisheta jiya ma ban shiga na gaisheta ba." Umma ta harareta kafin tace"ni ce yar aiken ki? In ko da Amana bai kamata Ruwa ya Dafa kifi ba, ace kina gida nan ki yini baki iya leka innani acikin gidan nan ba." Sultana ta tura bakinta gaba kafin tace"Umma ban samu lokaci ga makaranta ga kula da Ummi." Umma ta kalleta ta watsar ta yi ficewarta ta bar sultana ta kunkuni ita ya zata yi? Ko dame ake so taji. Ba sosai yanzu ta ke zuwa bangaren Innani ba tunda ta fara rashin lafiya sai taga dama. Kuma in ta shiga a tsaye ko zama bata yi, Ita kanta Innanin ta san cewa Sultana ta sauya ita saboda ta kanta ta ke yi bata cika ma damuwa da ita ba. Washegari da Safe Umma tace Sajida ta dauki Farida su je gidan sultana su gyara mata gobe jumma'a zata koma gidanta. Sajida ta kalli Umma cikin mamaki kafin tace"Umma ni kuma? Umma tace"To da wa zan saka? Ku tafi da wuri saboda ku samu ku gama gyaran akan lokaci." Sajida tace"Umma idda fa na ke yi? Kuma a musulunci ni matar Yusuf ne har yanzu" Umma tace"Kaniyarki da Iddan, ina saka ki aiki kina cemin kina Idda ne, in matarsa kike me ya zaunar da ke a gabana! Da sai ki zauna gidan Yusuf din ki gama Iddar taki." Ranar Sajida da kuka ta fita, Sultana na daki ta na jinsu ta na dariya. Lokacin ma tana waya da kanwarta ne mai bi mata. Tana fad'a musu zata zo in Yaya Sadiq ya zo ya koma zata zo ta yi sati a shinkafi. Sajida ba ta da mafita dole ta yi abunda Umma ta sakata. A gidan Sultana ita da Farida sun ci aiki Tunda gidan ya ji ma kulle duk ya yi kura. Suna cikin aikin Sadiya ta kirata tace gata nan tazo gida Umma tace ta na gidan Sultana suna gyara. Sajida tace"Sadiya kinga yadda Rayuwa ta yi dani ko? Na zama yar aikin Sultana ina yayar mijinta na koma kamar kanwar mijinta." Sadiya tace"Tabdijam, Allah ya kyauta." Da Sajidan tace Sadiyan ta zo nan gidan su had'u sai ma ta tayasu sai tace megidanta ya yi tafiya daga kasuwa ta biyo gidan Umma gida zata koma zata yi masa girkin Tarba. Kiri kiri Sadiya ta wucewarta gida kuma Umma ma da ta yi mata mgana haka tace mata. Sultana kuma Saloon taje bayan ta dawo ta biya gidan kawarta ita ta rakata gidan kumshi aka yi mata. Sai Yamma Sajida ta dawo sun gaji ita da Farida. Suna dawowa ba dad'ewa Sultana ta Dawo Umma na ta fad'an ta yi dare ga jaririya a bayanta. Kai Tsaye tace"Umma kunshi fa naje, haka zan koma jiki fari." Umma ba ta yi mgana ba Sajida ma da idar da sallah bata tanka mata ba. Umma taso ta tusa ma Ummi sai taga ta tashi tace zata shiga wajen Innani daganan ta wuce shashen Abba. Mama bata nan suna kano bikin diyar kanwarta bangarenta kulle ya ke ba kowa. Kawai sai ta isa gaban Sajida ta mika mata ta na fad'in"Anty Sajida ga yarki, ban yi sallar azahar ba ballatana mangariba." Ko kallonta Sajida bata yi ta mike lokaci daya ta na fad'in"Salla zan yi, kin ji an fara kiran sallar isha'i." Daga haka ta kabbarta salla tabar Sultana tsaye rike da yarta. Ai ko ta gane bata da wayau domin Sajida na gama sallah ta mike ta shige ciki gashi taki yin shuru sai kuka ta ke yi damam kuma sultana bata saba ba, ta saba Umma ke mata reno ko Sajida yau kuma ba ko d'aya. Duk ta yi wani yarkace yarkace da ita, A fusace ta shiga dakin ta iske Sajida kwance ta na Buga game a wayarta. Kusa da ita ta tsaya ta na fadin"Gaskiya Anty Sajida baki da imani, kina jin yarinyar nan na kuka ammh kin kasa zuwa amsheta ki lallasheta sallah fa nace miki zan yi gashi har an yi isha'i." Sajida ta dago cikin mamaki ta na kallon Sultana kafin tace"Ke ni sa'ar ki ce? Ko don kinga ina rage miki wahala shine zaki maidani kamar wata baiwarki? Yau din ma aikin Uban wa naje na yi ba naki ba? Gabadaya jikina ciwo ya ke yi gidan nan naki bayan kura harda tsohon dattin kazantar da kika saba, nagaji ba daukarta da zan yi gwara tun wuri ki goya yarki ki kama Hidimarki kin ji ma na gayamiki." Ta fad'a na juya mata baya Sultana ta kalleta rai bace kafin taja tsaki ta wuce. Sajida ta mike ta na fad"in"Kan bu, Sultana ni ki ke ma tsaki?. Sultana ta fice daga dakin tana fad'in"To haka kurun me kike yi? Daga nace ki taimake ni ki rikemin yarinya sai ki fara zagina, ni nace a sake ki da zaki wani Huce a kaina." Sajida mamaki ya sandar da ita a zaune ta ciji yatsa sannan ta girgiza kaj lalle yarinyar nan bata santa ba ne sai ko ta gyara mata zama. Kanwar dai naki dole Sultana ta goya yarta ta yi sallolin da ke kanta. Sajida barcinta tayi bata san shigowar Sultana ba cikin dare Ummi na ta tsala kuka tana jin Sultanan na kiran sunanta ta yi mata  banza Acikin ranta tace shegiyar yarinya mara Mutumci. Washegari tun safe Umma tace Sultana ta shirya ta maida ta gidanta Anty Surayya ta zo, Sajida kamar an matsi bakinta ta kwashe rashin kunyar da Sultana ta yi mata ta gayamata. Surayya ta kama baki kafin tace"Ita sultanan? Sajida tace"Wlh ita fa Big sis ai bata da kunya shegiya da kauye ta girma da naga karyan tsiya ni ce zata rika sakawa aiki kamar ta samu wata jaka? Surayya ta yi dariya bata ce komai ba sai dai ta bama Sajida Hakuri tace ta kama girmanta zata yi ma Sultanan fad'a. Koda suka tashi tafiya Sajida kin zuwa ta yi, zamanta ta yi a gida daman kuma Yusuf ta ke yi ma nacin don Allah yazo su hadu ita ta bashi Hakuri ya maidata dakinta kafin ta gama Idda tagaji da wannan bala'in yarinya karama ta fara raina mata wayau. Ta tuna kwanaki har sata ta kulla mata wai an sace mata 1k acikin jaka to waya sace ita ko? Tunda su biyu ne acikin dakin. Abba shi ya  ba da kudi aka yi ma Sultana duk cefanem da ta ke Bukata, Umma da Anty Surayya ba su dade ba suka barota Bayan Surayya ta ce ta tashi ta yi girki domin tarban mijinta Tunda ya taso yace yana Hanya. Suna fita ta koma ta kwanta ta na bama yarta Nono ta na kuma Chart. Ita fa bazata iya ba ta na zuwa shinkafi zata Dauki Naja kanwarta ta so ta rika taimakamata. Sadiq kuma da yamma ya iso gida ya fara Sauka sai a lokacin suka had'u da Sajida. Kallon kallon suka yi ma juna afalon Umma kowa ya dauke kai. Sai shine ya kalleta kai tsaye kafin yace"Sannu Sajida ashe kuma abunda ya faru kenan? Allah sarki zawarci ba dad'i ga shi daman kin tsani bazawara." Sajida ta kallesa ta san mgana ya gayamata, kuma ba laifinsa ba ne da kunya ma ta maida masa martani. Kasa mgana ta yi kanta na kasa tana Tunanin zama bai ganta ba. Umma ke tambayan su Hasiya da yara sai ya ke fad'a mata suna Zariya taje karbo Result dinta daganan zata je can garin da Mahaifiyarsu ta ke ta Dubata. Umma na zaune tace"Allah sarki, kwana Biyu bamu yi waya ba, ba na samun zama sosai Ga Innani ga Kuma Mama bata nan sun je biki." Sadiq yace"Umma jikin Innani na kara Rikicewa? Yanzu fa na shiga ta na dai kwance ammh ba wannan kuzarin da karfin jikin nata irin na baya? Umma tace"Ai innani jikin girma ya kwanta Sadiq, yanzu fa komai fa sai an yi mata jikin ya riga ya gama saki gabadaya." Sadiq yace"Umma zan yi mgana da Abba za'a siya mata keken da zata rika zama a kanta ammh kwanciyar nan ai bata da dad'i." Umma ta yi na'am da shawaransa sosai shiyasa yace zai tafi gidansa da Daddare zai dawo su yi mgana da Abba. Yana fita gidan ni ya kirani yana fad'amin ya sauka lafiya. Ni kuma lokacin ina gidan Adda Fati kwanan mu Biyu da zuwa ni da su Asim. Sai na gama cuku cikun karb'an Result sannan zan karisa wajen Amma. Shi ya ke fad'amin Umma na Cigiyata sai naji kunya nima kwana Biyu ban nemeta ba. Muna gama waya dashi na kirata muka gaisa har na bata su Asim da suka fara mgana Umma rad'am a bakinsu. Bayan nan mun yi mganar jikin Innani da ita, Innani na ran Assadiq koda yaushe sai ya yi mganarta har ce min ya yi ba domin kada Abba yace ya Dauke masa uwa ba da ya kawomin Innani wajena saboda gani ya ke a gabansa za'a fi kula da ita sosai. Sai na koma ina gayama Adda Fati yanayin jikin innani, tunda gidanta na sauka ban je gidana ba. Cikin Tausayawa tace"Allah sarki Allah ya tashi kafadanta, ni ko ina ita abokiyar zaman taki ta yi arba'in ko? Kai Tsaye nace"Eh sun gama wanka naji Assadiq na mganar." Adda Fati tace"Har yanzu baku da daidaita a tsakanin ku? Nace"Babu kam," Adda Fati tace"Ki kyaleta ki dai ki yi mata zaman da musulunci yace." Cikin mirmishi nace"To ni miye nawa? Da ba waje daya muke zaune ba." Adda tace"Shikenan ma kowa ya Huta." Mun cigaba da Hirarmu ina ba ta Labarin yadda sultana ta min wulakanci sanda na kira na yi mata barka. Ammh ban bata labarin abunda ya Faru sanda muka je gusau ba, ko bakomai akwai sirrin da zan Boye musu saboda bansan me gaba zata Haifar ba. *** Wannan karon dai Sultana ta yi abun arziki ba korafi da Rashin kunya sai ga Assadiq da yin kwanaki Biyar sannan ya biya ta Zariya ya Dauki siya da yara suka koma Abuja. Kuma Sultana ta nemi izinin zuwa shinkafi yace taje ta ga yan'uwanta da iyayenta jin dadinta ma ya bata kudi masu tsoka a hannunta. Yana tafiya ta fara shirin zuwa Shinkafi Umma ma ta yi mata Shiri sosai Abba ya ba da Motarsa Direba ya kaita tare da kayan abincin da zata kaima iyayenta. Sati cur Sultana ta yi a shinkafi an samu ta leka gidajen su Baba Sammani ta kai musu Ummi ta kuma gaishe su. Taji dadin zama acan tunda ba ta wani Wahala ga kannenta na tayata Renon Ummi daga barci sai chart kadai ta ke yi, Da ta tashi dawowa motar Haya ta shigo ta dawo kuma tare da kanwarta Naja da ta gama Jssce zata shiga SS. Mallam bai amince ba sai da ya kira Sadiq suka yi mgana. shi daman tace saboda zata rika taimakonta da Ummi ne ga makaranta da aikin gida. Kuma ganin kanwarta ne yasa ya amince. Sai dai Umma ta ganta da yarinya, Ba ta ce don me ba? Sanin halin Sultana yasa Umma bata ce komai ba. Gidanta ta koma tunda da Farko Sultana taso ta kara shantakewa a gidan Umma ita kuma nace bata isa ba, in tsoro take ji ga Naja nan sannan zata rika taimaka mata. Dole ta koma gidanta ammh kuma duk Ranar da tazo sai sun yi tanka tanka da Sajida. Da yanzu duniya ta gama yi mata zafi kiris ya rage ta gama idarta shuru ba Yusuf. Kwanaki ma taji an ce aure Mahafiyarsa zata yi masa gashi ya hana ta ganin ya'yanta kamar ma daga baya blooking dinta yusuf din ya yi. Ta fara nadaman Hallayanta Tunda su su suka kaita suka barota. Biyar yanzu ya fara gagaranta Sadiyan da suka fi shakuwa bata bata ko sisi,  Big sis ne kuma ta ke da tabbacin zata bata kudi ammh kunya bazai barta ta yi mata mgana ba. Ko Anty subai ta kasa kira tasan da ba domin ta sire a idanuwan Sadiq ba tana da tabbacin wlh shi zai kira Yusuf ya yi kokarin daidata su kuma bazata shiga talauci haka ba. To ko'ina ta bat'a garinta da Kunya a ga ta koma ta na yar murya Siyama kuma sun tafi lagos yawon Bude ido ita da mijinta. Abubuwa goma da ashirin sun yi mata yawa da ta rasa yadda zata yi. ******* Bayan wata daya, tuni Sajida ta fita Idarta yanzu ba matar Yusuf bace ita. Abunda ta ke tunanin bazai Faru ba sai gashi ya faru ta na cikin Layin zawarawa. Ta yi kuka kamar ranta zai fita ba mafita karshenta ma ranar da ta fita Idda aka Daura ma Yusuf aure da Budurwa yarinya karama Sakeena ta kirata ta na fad'a mata kamar Zuciyarta zata Buga haka take ji. Abba kuma yace abunda ta zab'ar ma kanta kenan Allah ya ba da sa'a. Umma ma tace shiyasa akace zaman lafiya ai yafi zama dan sarki. Saboda Halin da ta ke ciki yasa ta koma ta na zuwa gidan Sultana ta yini, ko da ba ta nan ta na makaranta ita da Naja ita ke zama a gidan ta na yi mata girki..saboda acan Umma bata sakar mata Fuska kwata kwata bata jin d adin zaman gidan. Ga shi Sultana ta yi ta mata wukalanci da gadara ita mai gida duk ta shanye. A watan da Sadiq yazo ya iske Sajida a gidansa sai da ya yi mamaki. Sai yaji kuma ta bashi Tausayi Kuma wannan ai ba girma ba be ki koma kina bin matar kaninki. Shiyasa da kansa ya samu Umma ya yi mata mgana. Ya lallasheta da Kaddara ne bawa bai isa ya sauya ta ba. Yace Sajida ta koma gida ta zauna gaban Umma ya kuma Dauki kudi 10k ya bata tare da ce mata in tana Bukatar wani abu ta kirashi. Naka naka ne, duk abunda Sajida ta yi masa yayarsa ce kuma shi ba Murna ya yi da Farko ba. Yaji dad'in yadda Allah ya nuna mata Ishara ammh bai taba Tunanin Yusuf zai rabu da Sajida haka ba ya Dauka na gargad'i ne daga baya zai maidata. Shi kanshi yaji mata rashin dadi sosai. Sai ga Sajida na kuka a gaban Sadiq kunyar duniya duk ya kamata. Ko sadiyan da suke had'a waje tare da ita ba ta tsinana mata komai ba. Kowacce na gidanta ta rike aurenta ita kuma ta na zawarcin da ta ke ganin kamar da gangan ne in mace ta zama bazawara ko auranta ya Mutu. A baya tana ganin abun Fahari ne A gareta tana ganin Hasiya kamar wata ba mace ba tunda Sadiq ya aureta a matsayin bazawara. Tafiyar Sadiq a satin Sajida ta kusa yi ma Sultana dukan tsiya. Wata ranar laraba ne sultana ta dawo makaranta sai ta Biyo nan gida. Daman nan take sauke gajiyanta. Umma bata nan ta na shashen Innani ita da Mama. Sajida ne kadai a falon Umma ta na zaune tana gyaran kumbunanta na kafa. Da farko da ta shigo sun gaisa har ta Dauki Ummi hannun Naja. Ita kuma taje ta zubo musu abinci ruwa ne tace Naja ta shiga kitchen ta Dauko musu. Bayan la'asar haka sai aka yi baki Siyama tazo da yan'uwan mijinta su gaida su Umma da Innani. Daga bangaren Mama suka zo bangaren Umma. Ga mama ga Umma a wajen, wata cikin yayar Baban Mijin Siyama suke gaisawa da Sajida. Kamar an Tambayi Sultana ta yi karaf tace musu"Anty Sajida ce bazawarar gidan mu ba." Gabadaya sau aka bita da kallo bata damu ba ta cigaba da fad'in"Yanzu shikenan kiri kiri Abban su Amal ya ki maida ke dakin ki? Gaskiya bai kyauta miki ba yasa kin zama bazaawara Anty Sajida ni kuma kunsan na tsani zawarawa yawancin su Yan bariki ne masu kwacen mazajen wasu." Umma kunya duk ya kamata Sajida kuma sai da taji ba ta taba muzanta irin na ranar ba. Matar ko cikin Tausayawa tace"Allah sarki, ai ba yin kanta ba ne shi kuma sha'anin aure ai na Allah ne, sai kiga kuma an daidaita a gaba. Kuma da kike mganar zawarawa yan bariki ne ni na kulubance ki ta wannan bangaran ba haka ba ne, duk wacce kika ga ta zama bazawara ba yin kanta ba ne kaddarace ta fad'a mana, kamar ni anan mutuwa ce sila wata kuma zaki ga sakin na kaddara ne ba macen da zata so ta zama bazaawara da son ranta karya ne wannan burin kowace mace ta zauna a gidan mijinta lafiya lau, saboda haka zawarci ba aibu ba ne sannan ki sani kaddara ce ke maida mace hakan." Umma da Mama har suna had'a bakin fad'in"Hakane wlh." Matar ta cigaba da fad'in"Kuma mganar zawarawa duk yan bariki ne wannan karya ne, ke yarinya ce karama daga ganin ki baki san rayuwa ba har yanzu, ni nan shekaran mijina Goma sha hudu da Rasuwa ban yi aure ba, to ina zani gani da ya'ya mata a gaba na? Sannan ba wai bam samu maneman ba ne na samu kawai ban yi ra'ayin auren ba ne kuma Alhamdulillah na tsare kaina sannan na tsare mutumcin ya'yana ba Kasawa bace domin an saki mace ba, Kaddara ne ta Ubangiji da in yace kun yafakum ba wanda ya isa ya dakatar da hakan, sannan domin bazawara ta sake wani auren ba kwacen miji ba ne cika sunar ma'aiki da kuma kare kanta daga zargin mutane ko fad'awa halaka, sannan ki sani itama bazawara mutum ce kamar kowa kuma Cikakkiyar mace maj yanci kamar yadda Budurwa ke da yanci. Ba Inda Allah ya ware budurwa da bazawara duka sunansu mata, kuma suma sun canchanta su samu farinciki wasu zaki ga sanadin hatsarin mota suka rasa mazajensu! Wasu kuma sanadin mutuwar Fuju'a wasu kuma sanadin Boko haram, wasu kuma sanadin Sakin aure da In Allah ya kaddaro ma mace ba ta da yarda zata yi, ya kamata ki daina Dariyan kaddaran zawarcin wata macen saboda ke ma macece kuma hakan ba abun mamaki ba ne in ke ma ya faru da ke watarana." Sultana duk sai ta raina kanta Sajida ko hawaye wani na bin wani a kan Fuskata cikin kuka tace"Wlh kina mgana kamar da ni ki ke, nima a baya ina daukan duk macen da ta zama bazawara wata mara gata ko wacce da gangan ta bari hakan ya faru, sai na ke ganinsu kamar ba su kaimu zama mata ba, sai da abun ya faru da ni na kara gane rayuwa na kuma san cewa Mace ba ta siyan ma kanta zawarci sai idan Allah ya kaddaro mata." Irin kukam da Sadija take yi sai da ta bama Umma da Mama tausayi. Umma a ranta itama sai taji kamar da ita ake yi, itama ai ta kyamaci bazawar sanda Sadiq ya kawo Hasiya. Gani ta ke yi kamar gazawa ce ke saka auran mace mutuwa. Ashe ba haka ba ne, Komai na Duniya nan Allah ne ya ke tsarashi kuma ya faru a yadda ya ke so. Matar nan har suka fita Sajida na kuka Umma da mama suka bi bayansu zuwa bangaren Innani. Suna fita Sajida ta mike sai ji ka ke tas! Tas ! Sajida ta wanke Sultana da maruka har Biyu cikin bacin rai ta nuna ta da yatsa ta na fad'in"In kika kara kokarin tozartani acikin mutane sai na yi miki Bugun tsiya sultana, tunda sakara kike mara kunya." Sultana Dafe da kunci ta na kallon Sajida kafin tace"Kika mareni Anty Sajida? Me na yi miki? Sajida tace"Uban ki kika yi min? Nace ubanki kika yi min" Sultana ta mike jikinta na rawa ta nuna kanta ta na fad'in"Ubana kike zagi? Sajida tace"Shi na zaga wannan tsoho mai gemu da ke zaune a kauye shi na zaga maras mutumci." Sultana ta saki shewa kafin tace"Wlh ba ubana ba, sai naki Uban, tunda uba bai fi Uba ba, kuma kada ki kara marina akan gaskiyata ba karya na fad'a ba da gaske ne ke din bazawara ce second Hand....! Ai bata gama Rufe baki ba Sajida ta Buge mata baki ta na fad'in"Ke ce zaki sama second hand da ikon Allah Sultana ba ni ba, ban da an cusa ma Sadiq ke mai zai yi da ke? Banza kucaka kazama wacce bata san ciwon kanta ba.!" Sultana na duba bakinta ta ga jini sai ta fashe da kuka tana fad'in"Kika fitar min jini? Wlh sai na rama kuma eh din ance bazawara second hand ce ni ai kuma ko da cusani aka yi da aurena mijina bai sakeni saboda bani  da hali mai kyau ba kuma kowa yasan halina ba na had'a husuma kuma ba na yad'a sharri." Sajida ta nuna kanta ta na fadi'ib"Ni ki ke fad'a ma wannan mganganun ina yayar mijinki? Sultana tace"An fad'a miki, ai ke ba uwata bace da zan ji kunyar gaya miki mgana." Sajida tace in ba zane Sultana ba ita ba yar halas ba ce..kawai ta Rufe Sultana da duka itama ta na kokarin ramawa. Umma Mama na shashen Innani Naja taje ta kirasu Allah yasa bakin sun tafi a haraban gidan suka ci karo da Siyama ta dawo rakasu. Suka dumguma bangaren Umma suka iske Sajida ta haye ruwan cikin Sultana ta na jibga. Ga Ummi na kwace kan kujera kamar ta sani ta na tsala ihu. Dakyar su Umma suka rabasu. Sultana fuska ta kumbura baki da Hanci ya fashe ita kuma Sajida duk sultana ta cijeta ta yakushe mata jiki ta kuma yagamata riga. Sannan ta riga jan gashin kanta har tana Cire mata tsinke kitson ta gashinta guda d'aya. Umma cikin bacin rai ta kallesu kafin tace"Me zan gani haka? Sajida abun kunya da kanwarki kike dambe? Sajida na haki tace"Na rantse sai naci Uban yarinyar nan". Sultana na hawaye tace"Ba dai Ubana ba." Siyama na gefe tace"Sultana baki da gaskiya miye haka? Mama na gefe tace"To kana karami ma ina kai ina rashin kunya?.. Inaga tun mganar dazu ne ke sultana baki kyauta ba kamar tozartata kika yi." Umma dai takaici ya hanata mgana ta koma daki ta zauna ta yi Tagumi. Sultana kuma ta saka kuka tace an had'e mata kai saboda an ga ba gidan Ubanta ba ne. Ta tattara kayanta da yarta ta tara Naja suka tafi. Ita kuma Sajida na yi ta mata Fad'an ba girmanta ba ne ta tsaya ta na biye ma Sultana har ta kai su ga Dambe. Siyama ma tace abun ba tsari. Kuma daman Sultana ta zama mara kunya yanzu. Sajida na kuka ta na gayama Mama da Siama irin tozarcin da Sultana ta dad'e ta na yi mata. Su kansu sai da suka ga bakin Sultana suna mamakinta Aure ne ko iskancinta ne ba su san abunda ya sauya ta ba. Umma ta kasa ko yi ma Sajida mgana saboda Haushi. Sai da Sajidar ta sameta ta bata hakuri sannan ta gayamata duk abunda ya faru. Umma tace"Uhm sultana sai shirin Allah, bai kamata ki zagi babanta ba tunda uba bai fi uba ba, bacin rai da kika Biye mata kina gaba da mijinta bama ita ba, ba girman ki ba ne ki zauna kina fad'a da ita." Sajida tace in sha Allahu bazata kara ba. Mama dai kusanta da rariyan baki ita takwashe labari ta gayama ya'yanta. Surayya kuma Sajida ta je har gidanta ta na kuka tana gayamata abunda ya Faru. Surayya ta yi ta ma Sajida fad'an wani irin raina kanta ta yi da Sultana zata yi dambe da ita? Surayya tace"Ba ga shi nan ba, ina gaya muku gaskiya ke da Sadiya kuna gamin ina kare ma Sadiq ba, ai gashi nan ta nuna muku halinta, daman ina amfamin Babba ya rika shigema yaro da sunan ba shi shawara? Wlh daman nasan haka zai faru." Sajida na kuka tana fadin"Wlh naga abunda kike fad'amin a baya, don Allah ki kara bama Sadiq hakuri, Hasiya ma ki bani lambarta zan kirata na bata hakuri." Da Farko Surayya taso ta Fattaketa ne sai daga karshe taji Tausayinta sosai.. Tace ta zauna gidanta ta kwana Biyu ta huta. Sadiya ma da taji sai jikinta ya yi sanyi tace Lalle Sultana ta zama yar iska mara Mutumci. Ta kirata a waya tanaa mata fad'an abunda ta yi bata kyauta ba sultana ta kashe mata waya. Wato ba ta da Lokacinta Sadiya da zuciya ta shirya ta bita har gida ta mata Tas tace taji kunya. Taje ta nemi wasu dangin tunda kuma ta raina gidan ubansu kada ta kara ganin kafarta a gidansu. Sultana ta rika kuka tace sun ci mata Mutumci kawai sai ta shirya kayanta Bata so taje shinkafi Tunda ba mai yarda da ita acan. Kai Tsaye batare da sanin kowa ba Washegarin Alhamis ta je tasha ta hau mota ita da Naja da Ummi sai garin Abuja. Suna sauka ta daga waya ta Kira Sadiq tace gata a Abuja yazo ya Dauketa. Yana Office ne zaune ammh sai da ya mike cikin mamaki yace"Abuja kuma?to ke da waye? Kai Tsaye tace"Ni da Ummi da Naja." Saboda tsabar mamaki sai da yavce"lafiya kuwa? Kin manta na fad'a miki gobe ina hanya tafe? Cikin gatsali tace"Ina sane, wulakanci aka yi min acan shiyasa na taho wajenka in kuma kaima zaka wulakantani ne shikenan sai na san inda zani." Bai Tsaya wani Tunani ba yace su tsaya a inda suka sauka gashi nan zuwa yanzu. Har ya dauki mota ya fita yana tafe yana mamaki da Tunanin me Sultana ta zo yi a Abuja? Yana hanya ya kira Umma yana gayamata ga sultana tazo Abuja ita kad'ai me ya faru? Umma kai tsaye tace"To ina zan sani ni tunda ba ta daukeni uwarta ta gayamin gata zuwa ba? Sai ka je ka sameta in ka tambayeta sai ta gayamaka abunda ya kawota." Daga haka ta kashe waya daganan yasan ba lafiya. Shi tunaninsa  yana zaman lafiyansa da iyalansa zuwan Sultana zai iya lalata masa yar natsuwarsa. *Janafty* *TMWB3K019* *TMW is a paid Novel, Pay 500 for regular or VIP N1K, Via 0552179550 Jamila Umar Gt bank, 09069067488* ‎Open this link to join my WhatsApp Group: https://chat.whatsapp.com/IhAz8h8nRy250ZnGGXwM65 A Jabi suka sauka na cikin Abuja shiyasa ya d'an dauki Lokaci kafin ya karisa, Sultana kuwa sai kiransa ta ke yi yana ce mata gashi nan bisa hanya. Ya yi mamakin ganin Sultana yarkace yarkace kamar wata yar gudun Hijira daga ita har yar Rakiyan nata daga gani sun sha wuya. Ummi ma sai rigima ta ke yi, Sultana uwar banza ce son jiki ya yi mata yawa wai Naja ta mika ma Jaririya ita ta na tsaye kamar wata sakara. Shine ma ya yi saurin karb'an Ummin a hannun Naja ya kuma karb'i kayansu ya saka a bayan mota. Da Mamakin Akwatin da yaga Sultana ta kwaso ya bude mata gidan gaba ta shiga ta zauna Naja kuma ta zauna a gidan baya. Sun fara tafiya ya mika mata Ummi yace ta bata nono ta na kuka, ta karb'eta ta na tura baki. sai alokacin ya lura da kumburin fuskarta na Fad'an da suka yi da Sajida. Cikin mamaki ya kalleta kafin yace"Me ya same ki a fuska kuma? Kallonsa ta yi kafin tace"Bakomai.." Ta fad'a lokaci d'aya ta na kauda kai can garin kalle kallenta Nono ya shake Ummi ta fara tari. Sadiq ya fara yi mata fad'an meyasa ita ba ta kula ne? Cikin gatsali tace"to ba ita ta shake da kanta ba." Cikin Hararanta yace"Da ta shake ke kuma uwa mara kula ko? Haka ake ba yara Nono? Kin sakar mata shi yaushe ta saba ballatana ta iya rike kanta, duka duka yaushe aka haifeta? Ya kamata ki rika lura Sultana kin girma tunda ki ka zama uwa yanzu." Tura baki kawai ta yi bata yi mgana ba, sai shi nw ya nuna mata yadda zata saka Ummi a saman kafad'anta ta jijjiga ta na Buga bayanta tare da Hura mata kanta zuwa wuyanta. Tana yi kuma ta na tura baki a Fili ya Furta"Allah ya sauwake miki, da kike son ki haifi yan biyu in da Allah ya baki na tabbata wlh bazaki iya renon su ba  tunda ga shi guda d'aya ce ammh ta gagareki." Da Sauri Sultana tace"Ai ko zan iya." Kallonta ya yi ta kasan ido a rene kafin ya maida hankalinsa kan Tukinsa. Batare da ya kara kallonta ba yace"Me ya faru ne a can gusau kika taho ba wanda ya sani.? Kallonsa ta yi kafin tace"Umma ta sani mana." Kai tsaye yace"Bazaki daina min karya ba ko Sultana? To na yi magana da Umma kafin na zo nan kuma ta tabbatar min bata san kin zo ba." Sai ta kifta ido kamar wata barauniya sannan ta wani tura baki kafin tace"Gidan mijina ne sai na nemi izini zan taho.? Kai tsaye yace"Gidan ki na can gusau nan gidan Siya ne, kinsani kuma." Hararansa ta so ta yi sai taga yana kallonta sai kuma ta fasa ta koma ta na sunne kanta kasa kamar wata munafuka. Suna tafe a mota ya tuna bai kira Siya ba, kuma bai kyautu sai dai taga baki kawai ba sanarwa ba. Nan take ya rage gudun motarsa ya Dauki wayarsa ya kirani. Lokacin ni kuma ina zaune a falo Tibi na aikinta da Mbc3 Cartoon saboda su Asim. Waya ce a hannuna tunda yanzu saboda zaman kad'aici yasa na waye da sanin Kafafen sada zumunta. Ina yin Faceebook har da Instagram, ina cikin Groups sosai na karuwa na ganin abunda ke faruwa a duniya. Ina cikin Sirrin y'a mace a Facebook, sannan Ina cikin Arewa open diary, sannan a Intagram ina cikin Northenhabiscuss. Ina ganin abubuwa sosai kuma ina karuwa na sha kuma cin karo da ma su irin abunda ya danganci Rayuwata. Daganan na Fahimci yanzu mutane sun maida Canfi dabi'an su. Sun kuma sakashi cikin Addini mun saki Allah mun kama mganganun jahilai da malaman tsubbu marasa tsoron Allah. Ina Tsaka da dube duben Labarai na ban aljabi da Tausayi da mamaki da yanzu na kware wajen bibiya kiran Assadiq ya shigo. Asim da Asif suna daga can gaba a kasan Cafet suna kallo rabi da rabi kuma suna wasa da Motarsu na roba irin na yara mai tafiya d'in nan. Da zumud'i na Daga kiran nasa ina mai Fad'in"Mijin Siya." Shima cikin Farinciki ya amsa min da cewa"Matar Assadiq." Wanda fad'in haka da ya yi sai da Sultana ta kallesa wani kishi mai zafi ya Turniketa. Wato matar Assadiq ita da kai Tsaye ya ke kiran sunanta ba Tausasawa a cikin kiran nasa  ammh kalli yadda ya ke mgana da Matarsa cikin girmamawa kamar ta na gabansa Ya sha harara shi ko bai ko kalleta ba Rabin hankalinsa na wajen Siya rabi kuma na wajen Tuki. Cikin yanayin maganarsa yace"Ya gida? Da sauri yace''Gida lafiya lau, sai dai kewarka da mutanen gidan suka yi." Cikin yar Dariya yace"Nima na yi kewarku, ina su Asim? Na kallesu kafin nace"Ga su can suna kallo rabi kuma suna wasa kasan su.' Jinjina kai ya yi kafin yace"ke kuma fa? Ina dariya nace"Kasan ai abunda na ke yi ko? Shima dariyan ya maidamin kafin yace"Nasani kina nan kan waya kina Shige shigen da yanzu kika saba da shi." Mirmishi na yi ina kara fad'in"Kamar ka sani, ina can ina karanta wani Labari kamar irin nawa labarin, Mijin Siya na fara wani tunani fa" Da sauri yace"Tunanin mene? Ni kuma kamar nasan sultana na gefensa sai nace"sai dai ka dawo sai mu Tattauna mganar na Bukatar natsuwa gaskiya." Gyaran muryan Sultana yaji da yasa ya tuna da ta na kusa da shi. Shifa in ya na mgana da Siya ko yana kusa da ita ya kan manta da kowa da komai ne baya ganin kowa sai ita. Shiyasa ya yi saurin cewa"Ga ni nan zuwa gidan ma yanzu da baki, ki gyara dakin nan da ke kusa da namu don Allah." Cikin mamaki nace"Daga Gusau ne? Kai tsaye yace"Eh! Kin dafa abinci? Cikin zumud'i a zato ko cikin yan'uwansa ne yasa nace"yar sauran miyan jiya da ta rage dazu na Dafa Farar shinkafa naci, su Asim ma goldenmorn na had'a musu suka sha, bakin da yawa ne? Cikin sauri yace"A'a mutun biyu haka." Cikin Girmamawa nace"zai ishe su anjuma sai a kara dafa musu wani abun ko? Shima sai yace min eh, Kamar yana ganina haka na mike ina fad'in"Dakin ma bashi da wani gyara sai dai saboda kura bari naje na share na goge.' Ya amsa da"Allah ya yi miki albarka Siya, sai mun iso." Daga haka muka yanke kiran, Ta bangarena ban taba kawo ma raina Sultana ce ta zo ba. Tunda yace min suna hanya na Ijiye wayata na shiga dakin na fara gyarawa Gado ne kawai sai Wardrope sai cafet akwai Tiolet acikin dakinn. Ba mu tab'a kwana aciki ba sai dai muna saukar da baki in suka zo mana. Jiki na rawa na gama sharewa na saka Moper na goge ko'ina har Tiolet sai da na wanke na saka turaran Wuta a Burner mai kamshi. Sannan na fito na iske su Asim sun min barin madara a falo tunda nan saman Tv sand na dora shi. Sai na Musu fad'a na ce su hau kujera su natsu ina cikin goge cafet din ne naji Dirin motar Assadiq. Su Asim sun yi wayau sanin Karan Motar Babansu da gudu suka fita na bisu da kallo shiyasa nace a karshen wannan watan zan kai ma Umms su, tunda na yayesu a Boye batare da Assadiq ya sani ba Suna da wattanin sha tara kenan shekara Biyu, Assadiq ne ya hana in yaye su tun suna da wattani sha bakwai Na gama gogewa kenan ina fesa Turaren ruwa na Cafet naji Sallamar Assadiq. Na juya cikin Fara'a ina amsa sallamar nasa, sai dai bakina ya yi nauyi sanda na ga Sultana a bayansa sai wani mele baki ta ke yi Su Asim kuma Assadiq ya had'asu ya Dauke su, Yarinyar da ke bayanta ne dauke da Jaririyar nata. Nan da nan na shanye mamakina, na Saki Fara'a ina yi musu maraba. Na maida abun hannuna bayan Tv da ke falon na isa garesu ina yi musu maraba da zuwa. Na wuce sultana na karisa gaban Naja na karb'i Ummi daga Hannunta. Kuma na kalli Sultana ina yi mata maraba cikin Fara'ata nace"Sultana sannu da zuwa, maraba ku zauna mana." Assadiq daman shi ya samu wajen zama yana bidiri da ya'yansa, Sultana tak bata ce min ba kallo ma ban isheta ba, kamar bata so haka taje ta zauna a kujeren da mijinta ya zauna lokaci d'aya ta na kare ma falon nawa kallo. Tana wani tabe taben fuska kamar Taga kashi. Ni na karbi akwatin da Naja ta jawo ina rike da Ummi na shigar musu da shi Cikin dakin da Assadiq yace na gyara. Ina fitowa na isa gaban Sultana na mika mata Ummi da ta fara rigima ina Fad"in"Ki bata nono, Asim ba ku ga kanwarku bace? Na fad'a ina nuna musu ita, Assadiq yace"Ku je ku ga kanwar ku mazajen Abbu" Ya fad'a ya na nuna musu Ummi da ke hannun uwarta da ta had'e rai kamar taga wani abun ki. Ni kuma kitchen na shiga Dauko musu Ruwa na had'o musu Lemun Maltina da Fanta sai Ruwan Faro mai sanyi na sako a wani babban Faranti na kawo musu nan Tsakiyar falon. Naja center Table na tura gabansu a kai na sauke musu. Kuma na durkusa ina zuba musu tunda na had'a da kofunan glass. Naja na fara mikamawa sannan na mikama Assadiq ya karba yana min mirmishi ita kuma Sultana ganin ta ba ma yarta Nono sai na kyaleta da Niyar in ta gama sai ta zuba ta sha. Na koma gefe na zauna ina kallonta ta na Ture hannun Asim da ke wasa da Hannun Ummi. Asif kuma uban karambanin ya na neman haye jikin Sultana ya danne Ummi. Ina shirin mgana naga ta Tureshi cikin Tsawa tace"Kai baka da Hankali ne? Ban tashi ba ganin Assadiq ya kalleta cikin mamaki Asif jin an daka mai tsawa yasa ya tsorata shima Asim haka. Kafin kace me sun fashe da kuka ba su nufi wajen Assadiq ba sai suka nufo ni suna kuka. Na kama su na rike ina llallashin su ina fadin"baku san kanwarku ba ko? Ku yi mata wasa a hankali kun ji ko? Suna ta kallo na tunda suna jin mgana, suma ai suna mgana sai dai bata nuna ba ne, ammh sun iya kira sunan Abbu da Mami su san Umma da Abba da Goggo Surayya. Assadiq ne ke yi ma Sultana fad'a da cewa"Ina yaro kamar Asif yaga hankali sai ki yi masa a hankali Tunda yaro ne" Baki ta tura bata yi mgana ba, ni kuma ganin su Asim sun yi shuru sai na kwaso musu kayan wasan su nace suje su yi wasa. Lokaci d'aya ina kallon Assadiq kafin nace"Ko za su yi wanka ne kafin su ci abinci.? Kai tsaye yace"Gata nan tana jin ki." Ya fad'a lokaci daya yana mikewa agogon fatan da ke hanunsa ya kallah kafin yace"Zan koma Office akwai wani abun da kuke Bukata ne? Girgizamasa kai na yi alamun babu. Ita ya kallah yana jiran tace wani abu sai kawai ta kauda kai kafin tace"Ban ga dakin da zan sauka ba." Kafin ya yi mgana na rigasa da sauri nace"Laa ga daki nan, har na kai kayan ku ciki ma." Na fad'a ina nuna mata dakin da Hannuna ko kallona bata yi ba ta mike Dauke da ummi Lokaci d'aya ta na fadin"ta shi mu je Naja." Muna tsaye ta wuce cikin dakin Naja na bin bayanta. Shi dai kai kawai ya girgiza kafin ya wuce yana fad'in"Sai na dawo." Na rakasa har kofar falo sannan na dawo cikin falo. Na zauna na yi tagumi ina Tunanin yadda zaman mu zai kaya da sultana daga gani kuma ta zo ta jima ne, kuma Yadda ta ke nunawa har yanzu ba ta son zaman lafiya. Tunda Assadiq ya fita ina falo nan, saboda kula da su Asif, kada na tafi daki su yi min barna. Ammh su Dultana ba su fito ba ni dai ina ta jiransu saboda na basu abinci. Sai da naga har La'asar ta yi na tashi na koma daki na yi salla. Bayan na idar salla ne na kara Fitowa falo na iske su Asif na ta guje guje da Motocinsu har kuma Lokacin ban ji motsin Sultana ba. Sai na koma kitchen daman Shinkafar na cikin kula da miyar farantai na had'a da Cokula a faranti na had'a na dauka sai dakin da na sauki Sultana. Kofar ta na Rufe ne sai da na kwankwasa sannan Naja tazo ta Budemin ban shiga na mika mata Farantin hannuna ina fad'in"Ki zo ki daukar muku ruwa." Tace toh ta shiga ta ijiye ta fito Falo ta Dauki Farantin Ruwa da lemun da na zuba musu tun dazu. Kitchen na koma ina Tunanin abunda zamu ci da Daddare, Sai na yi tunanin na yi mana Tuwon shinkafa Miyar agushi da Nama. Nan da nan na zage na fara aiki Daman Saboda wayar zamanin nan na Koyi girke girke da snkas masu dama a kafafen sada zumunta da suka kara taimakamin sosai. Sai zuwa can Naji buruntu a falo da na leka sai naga Naja ce goye da Ummi ta duka ta na ta taya su Asif wasa da Motoci ganinta yasa sai naji dadi nasan zata kula da su. Ina cikin yin girkin ne wayata a falo ta dauki kara ana ta kira ban ji ba. Sai da Naja ta kawomin tace ana ta kirana, ina Dubawa sai naga Umma ce ta kirani har sau hudu. Da sauri na wanke hannuna na bi bayan kiranta. Bayan ta dauka mun gaisa ta tambayi su Asim kai tsaye nace"Umma su nan zuwa a karshen wata nan, yaye zan yi musu sun kusa shekara biyu." Umma tace"Ma sha Allah, sai sun zo muna nan muna jiransu, ammh ki gayamusu kada su zo hannu Rabba na." Ina ta dariya Umma na tayani sai can ta kira sunana na amsa cikin Sanyin murya tace"Ashe kuma yau kun yi bakuwa ko? Kai Tsaye nace"Eh Umma suna nan tun dazu." Umma ta yi shuru kafin tace"To ki yi hakuri Hasiya, nasan halin sultana da Rigimar tsiya da sakarci duk abunda zata yi kada ki Biye mata, ni ban ma san tafiyarta ba yar hatsaniya suka yi da Sajida yasa ta yi fushi da kowa ta taho nan Wajen ku." Cikin mamaki nace"Subhanallah! Allah ya kyauta kada ki damu Umma lafiya lau zamu zauna har tagama kwanakinta ta dawo in sha Allahu." Umma ta yi ta sakamin albarka kafin mu yi sallama.. Na cigaba da aikina ammh a gefen raina ina mamakin wai sultana da Anty Sajida suka yi yar hatsiniya? Lalle abun da ya baka mamaki watarana shi zai baka tsoro. Ina da ganyen Allayahu da ganyen Ogun saboda Assadiq na san Abinci da ganye yana yawan siyomin ni kuma sai na saka masa ruwa na saka a leda na Masa masauki acikin Firiza. Ni kad'ai na yi aikina kamar yadda na Saba Sultana ko ganinta ban sake yi ba. Ammh naji muryanta a falo kamar ta na yi ma Naja mgana ne, sanda kuma na Fito ban ganta ba sai Najan tare da su Asif. Ba goyon Ummin kila uwarta ta karbe'ta ne, Sai da na yi sallar mangariba na zo na kulla Tuwon a ledan Naja kuma nace su bar wasan su yi sallah sai na kunna musu Cartoon nace su kallah na kwashe kayan wasan na kai su dayan dakin da ke kusa da inda Sultana ta sauka. Assadiq ya dawo ina wanka naji shigowarsa Bedroom dina sanda na Fito baya d'akin. Lokacin da Tada sallar Isha'i ne ya sake shigowa shima ya Shiga wanka. Na idar kenan sai gashi ya fito ina zaune saman darduma na yi masa sannu da zuwa ya amsa ya na kallo na kafin yace"Ya aikin? Ya baki kuma? Kai tsaye nace"Alhamdulillah.' Gayamin ya ke yi yaga su Asim sun samu abokiyar wasa naja, nace masa sai da na kwashe kayan wasan ai. Shima yau a gida ya yi sallar isha'i ni kuma na fita falo na had'a mana Abinci saman Cafet Tunda Assadiq ya fi son cin Tuwo a kasa fiye da a zaman kujerun zamani. Naja nace ta je ta kira sultana, yau ko su Asif ban samu yi ma wankan yammah ba kila sai munzo kwanciya, ni kuma na koma daki na taya Assadiq shiryawa cikin Saukakkun kaya na shan iska. Muka fito tare na iske Hakima Sultana ta shab'a uban ado, Ta zauna saman kujera kafa d'aya kan d'aya. Har ta zuba tuwonta ta cika Uban miya da Nama ta fara ci. Naja da su Asim na gefe suna kallon Cartoon. Mamakinta ya kamani sai dai ban yi mgana ba, Assadiq ne da ya zauna ya kalleta yana fad'in"Sultana shine baki jira mun zo an ci gabadaya ba." Ba ta ko kallesa ba tace"Ni da gidan mijina ba sai na jira wata sannan zan ci abinci ba." Ya kalleta cikin mamaki zai yi mgana na kateshi da kiran Naja da su Asim Su daman nasan ba su cika damuwa da abinci ba Tea suke sha ko kuma su sha Goldenmorn. Ammh na tattarosu na saka musu a filet d'aya har da Naja nace ta luramin da su kads su bata jikinsu da wajen. Sai tace min zata rika basu ma a baki. Abunda ya Hana Assadiq mgana kenan ya yi shuru kawai ya koma ya na kallon sultana Lokaci daya da mamakinta. Shi na fara zubamawa sannan na zuba ma kaina, tare muka fara cin abinci shine kamar ya tuna da wani abu ya kalli Sultana ya na fadin"Ina kika baro Ummi? Kai tsaye tace"Tana ciki ta yi barci." Cikin sauri yace"Ita kadai kika bari a daki? Ta tabe baki kafin tace"To me zai cinyeta? Saboda sanin halinta na rashin kunya yasa bai yi mata mgana ba. Muka cigaba da cin abinci, muna cikin ci ne aka kirasa a waya bansan waye ba naga ya bar cin abincin ya mike ya koma daki sai da ya jima sannan ya fito. Sai ya iskeni sai ni kaad'ai sai yara a falo Sultana ta gama ci ta tashi ta barmin filet da komai ta koma daki. Ina durkushe ina ta tattara kwanukan Naja na tayani Asif har ya yi barci Asim na kasa a kwance shima barcin zai yi. Kai tsaye yace"Ina sultana? Sai na nuna masa dakin da ido kafin nace"Ta koma ciki." A zafafe naga ya shiga dakin ya Rufe kofa, ban matsa ma kaina sai naji abunda ke faruwa ba. Tun kafin Assadiq ya gayamin Naja kanwar sultana ne na gane suna diban kama, sai dai ba Halinsu d'aya ba ita ba ruwanta ga hankali da taga zan yi abu zatace in kawo ta tayani. Tare da ita muka kwashe komai zuwa Kitchen na barta ta na gyaran inda su Asim suka ba'ata ni kuma na kwashe su Asim zuwa daki zan yi musu wanka. Har sun fara barci na shiga da su Tiolet daya bayan daya na yi musu wanka duk sun bata jikinsu da maiko da miya. Na gama saka ma Asim wasu kayan ina kokarin sakama Asif sai ga Assadiq ya shigo ransa bace. Bai yi min mgana ba ya shiga Tiolet sai ga shi ya fito sai kuma naga ya Bude dirowa ya dauko kayan barci ya koma Tiolet ya sauya. Ya sake fitowa ya gyarama Asim kwanciya a tsakiya ya gyara Filo zai kwanta. Sai da na gama saka ma Asif kaya na mika masa shi, shima ya kwantar da shi gefen dan'uwansa a tsakiya. Kallonsa na yi naga ya juya ya Rungume ya'yansa. Cikin mamaki nace"Assadiq ba anan zaka kwana ba fa? Da sauri ya kalleni kafin yace"Sai a ina? Kai tsauye nace"A dakin Sultana mana, ai kana wajenta har ta koma Bisa adalci ita ke da kai, ni daman ai muna tare dakai kafin ta zo." Shiru ya yi na wani Lokaci kafin yace"Yarinyar da ta zo da ita fa? Kai Tsaye nace"Ta zo dakina mu kwana tare, kaga ai bazata kwana a falo ita kad'ai ba" Sai ya jinjima min kai duk da yanayinsa ba dad'i haka ya mike ya Dauki wayarsa har ya kusa fita ya kara Dawowa ya Dauki karaman Computer dinsa ya fice bayan yace min sai da safe. Nima na rakasa da sai da Safe. Ina ga shi yace ma Naja ta shigo mu kwanta sai gata ta shigo nace taje ta yi fitsari tazo mu kwanta. Ni kan na dad'e ban yi barci ba akwai wani Tunani da ke yawo a raina Shi na ke ta nazari ba na so na fara yin wani abu batare da sanin Assadiq ba. Mun yi chart da Surayya ta ke tambayata ya bakuwa na ce lafiya. Bata gayamin komai ba sai dai ta kara tambayata ko Sajida ta kirani? Nace mata bata kirani ba. Daganan sai na kara Fahintar wani abu ya faru, wanda yasa sultana tazo kuma daman Umma tace an yi yar hatsaniya. Da asuba Assadiq ya tasheni sallar asuba shi kuma ya tafi masallaci. Saboda yana fita aiki in na yi sallah ba na komawa na ke fad'awa kitchen na sama masa abunda zai ci. 8am ya ke fita kafin lokacin kuma ya karya ya shirya, har kuma ya bar gidan Sultana bata fito ba abun karyawanta ma Naja na ce ta bita da shi Tunda ta zama Hakima. Ni bazan yi mata abunda tayi min ba, Ummi ma na goye bayan Naja tun safe, ko wanka ba'a yi mata ba ni na karbeta na yi mata tare da Asim. Ai ko da naja ta kaita a saka mata kaya ina falo ina jin Ta na yi mata fad'an Uban wa yace ta ba ni yarta? Salon aje a goga mata wani bala'in ko kashin tsiya. Da karfi ta rika yi saboda naji, ni kuma sai na yi kamar ban ji ba ta kuma tayi ma Naja kashedin kada ta  kara bani yarta in ta kara sai ta yi mata Duka tsiyan A raina nace abun bai kai nan ba, rike yarki ai nima na Haifa. Assadiq ya kirani yaji ko ba ma Bukatar wani abu? Nace ba ma abukatar komai. Ni kadai na ke Budirina acikin gidana sai Naja da yau ta hanata ma zaman Falo tare da su Asim. Komai na Dafa daki nake aikama Sultana taci kuma ta bar shi aciki sai zan yi wanke wanke na ke saka Naja ta shiga ta Daukomin. Haka na ke tafiyar da ita, tun kuma ina saka ran yau zai ce min zata tafi har naga ta kwarari sati ta na Hutu ina yi mata Bauta. Sannan ni da tazo gidana ne nice in ta fito na ke gaisheta ta amsa kamar ba ta so wani Lokacin sai in a gabansa ne ta ke amsani. Ranar da ta cika sati muna cin abinci da Daddare kai Tsaye ya kalleta yace"Yau dakin Siya zan kwana, ki tafi da Naja dakin ki." Dagowa na yi ina kallonsa sai naga ya had'e rai, kuma daman na lura tunda sultana tazo ba wani jutuwa tsakaninta da Assadiq. Shekaranjiya ina jin tashin muryansa kamar ya na mata fad'a ne. Kafin na yi mgana ita ta rigani da cewa'"Banga ne ba? Kai tsaye yace"Da hausa na yi mgaana ko baki jin Hausa ne? Baki ta tura kafin tace"Tabdijam wlh ba'a isa ba, ni da na zo kwanan nan ita ai anan take koda yaushe tare dakai in adalci zakayi min a dakina zaka zauna har sai na gama zama na tafi." Shima kai Tsayen yace"Shine na yi miki na fitan hakkin bakunta, sai ku raba kwana Bibbiyu, tunda naga kin wuce bakuwa yanzu kin zama yar gida." Ta kallesa ranta na suya ta gane take takensa so ya ke ta koma gusau kuma wlh ita taga waje bazata koma ba. Kuma ta fad'a masa kada ma ya Dauka wasa ne. Shi kuma ransa ne ke bace yarinyar nan ta mugun rainasa ya na mgana tana maida masa martani. Ya ji kunya da yaji wai Dambe ta yi da Sajida Surayya ta gayamssa Tun ranar da Sultanan ta zo. Kuma ya Tsareta ya tambayeta ta na kuka tace Sajida ce ta fara zagin Ubanta. Ya yi ma sultana fad'an baya son reni kada ta kara gigin fad'a da yan'uwansa in bata ci darajan suna yayyensa ai su ci Daraja suna yayyenta ita. Kuma ya yi hakame saboda kada ta kara kwatatanwa a gaba ammh a ransa yaji dadin haka. Yanzu sai Sajida ta kara gane bata da wayau, Tunda abokiyar shawaran nata yanzu itace abokiyar Fad'anta. Yace in ta yi sati ta koma Gusau ta saka masa kuka abunda yasa ya kyaleta ya bari sati na sama in zai tafi ko taki ko taso sai ya tafi da ita baxata zauna a gidansa ta hanashi zaman lafiyan da ya samu ba. Ni kuma gudun Fitinar Sultana yasa nace na bar mata kwanan nawa gabadaya har ta tafi. Shi kuma sai yaji Haushi ya fara min Fad'an meyasa na fara abunda ba Halina ba? Gaddama zan fara yi masa? Ina jin haka sai na yi shuru na koma ina bashi Hskuri. A fusace yace"Nan gidana ne, ku kuma dukkan ku mata na ne, kuma hukuncin da na yanke da shi za'a yi amfani na gama mgana." Sultana ko na jin haka ta mike ta rike Kugu ta girgiza jiki kafin tace"Tab wlh baku isa ba, in a can kun saba Tauyemin hakki anan ko ba wanda ya isa." Dagani har shi ita muke kallo, sai naga kuma hankalin Naja ya koma kanta sai na yi saurin cewa ta tafi da su Asim dakina su cigaba da wasan su acan ta na goye da Ummi ta rike hannayen su Asm suka tafi dakina Tunda sun gama cin abinci. Sai da suka shige sannan na kalli Sultana ta na wani cika ta na batsewa kafin nace"Ki yi hakuri, dakin ki zai rika kwana har ki tafi in sha Allahu." Cikin Fusata Assadiq ya kira sunana"Hasiya.." Na kallesa da Sauri ina fadin"Assadiq menene aciki? Ai ni muna tare dakai ko da yaushe ita kuma zuwa ta yi zata tafi nan da Lokaci kad'an" Kamar sultana na jirana sai ta harzukomin ta na fadin"Malama yi min shuru ba na son munafunci, har kina wani cewa zan tafi to ba inda zani nan gidam mijina ne ina da iko da shi kamar yadda kema ki ke da iko da shi." Ina jin haka sai na yi shuru, shine ya kalleta cikin bacin rai yana fadin"Na gaya miki zan sake fad'a miki kuma nan ba gidan ki ba ne, gidan Siya ne gidan ki na Gusau kin barosa." Sultana tace"Wlh bazan yarda ba ai gidan ka ne ba nata ba,nima ina da Iko da abunda ka mallaka Ehe." Cikin gatsali yace"ok tunda hakane kina son kwana da miji sai Siya ta baki girki shikenan' Siya daga gobe ta fara yin girki, ta bar kara miki walaha kin ji na gaya miki." Sultana ta Fashe da kukan kissa kafin tace"Wlh ni bazan yi girki ba, dame zan ji da Girki ko da Reno. Ni bazan iya ba" Kai Tsaye yace"Fine sai ki tattara ki koma gidanki, ki bar mata nata gidan." Cikin Dara kafa tace"Saboda me ka ke korana? Baka san na zo kusa da kai? Assadiq yace" saboda ba alheri ya kawo ki ba, in da zaki zauna lafiya da matata kibi Umarnina ko shekara zaki yi bazan damu ba." Sultana ta shiga mganganun cewa yace mata shed'an ita wani rashin Alheri ta kawo kaza kaza sai yi ta ke yi bai tanka ta ba. Ni kuma na kwashe abunda muka bata na kai kitchen na koma daki na basu waje suna cashewa yana mgana ta na maida masa martani kamar bata san Darajansa ba. Ko da na koma daki yara duk sun yi barci sai na gyara musu kwanciyar, nidai har na kwanta ina jin ta shin muryoyinsu a falo suna Rigima kai wannan yarinyar akwai rigiman tsiya. Da safe kuma ya kara Jaddamin Sultana zata yi girki. Ai bayan fitansa har 3pm na rana bata Fito ba maga zan yini da yunwa ni da yara na tashi na Dafa muka ci. Ba kunya da yunwa ta Ciyota sai ga ta fito falo muna zaune muna kallo Naja ta kallah kafin tace"Ke ina abincina? Ni yarinyar ta kallah tunda taga yau ban bata ba ta kai mata kamar yadda na saba ba. Naja ko tace ai ban bata nace ta kai mata ba, sai kawai ta Wuce kitchen ta na fadin"Ba wanda ya isa ya hanani cin abincin da mijina ya siyo ya kawo" Na so nace mata da ya siyo ai ban yi mata iyaka ba, gwara taje ta dafa da kanta bazan hanata ba. Ammh sai na Tuna da wani abu sai na yi kamar ban ganta ba. Kuma har na Daren bata girka ba, ni na girka shi da Assadiq ya dawo yaga bata yi ba zai yi fad'a na ce masa don Allah ya yi hakuri ya kyaleta ba girmansa ba ne ya Biye mata suna sa'insa. Da kamar bazai hakura ba sai kuma ya kyaleta, kuma na rokesa alfarman ya rika kwana a dakinta har ta tafi. Cikin Takaici yace"ta ce miki ta na da Niyar tafiya? Nima cikin mirmishi nace"Bakomai sai na bar maka kai, har sai ka Gundureta." Karamin Tsaki yaja kafin yace"Ban taba sanin yarinyar nan Fitinanniya ba ce sai yanzu acan ta gama yi ma kowa rashin kunya har su Umma bata bari ba, nan kuma zata zo ta hanani zaman lafiya" Ni dai sai na cigaba da bashi baki har yace zai saka mata ido. Tundaga ranar na dai binta da abinci acikin daki, sai dai ta fito in taji yunwa ta dib'a a cikin Kitchen. Kuma bata ganin girmana ballatana in samu arzikin ina girka mata taci. Gaisheni ma batayi sai dai ta shiga daki ta kwana da miji ta fito ta na Chab'a ado ta na isa da gadara ita adole gidan mijinta ne. Assadiq bai gayamin Abunda ya Faru Tsakanin Sultana da Sajida ba. Siyama ta kirani ta bani Labari tas, sai naji Tausayin Sajida har ga Allah na san zafin sakin aure sai naji kamar alokacin ya faru dani. Kuma na bama Sultana rashin gaskiya, komai lalacewar Sajida ta na da kimar da bazata iya maida mata mgana ba ballatana ta yi dambe da ita. Ammh Saboda bata da Mutumcin har Anty Surayya ma a halin da sultana ke nunawa zata iya sa'insa da ita, Siyama ta yi ta son taji ya mu ke zaune da Sultana? Bakina kanin kafana nace muna zaune lafiya saboda mene ita fa Sultana ta su ce, ni ce bare na zak'e watarana zata iya barewa dani. Sajida kuma bata kirani ba, ta kasa kirana Saboda kunya. Sai ni da kaina na kirata Tunda ina da Lambarta ashe itama ta karb'i lambata. Ina kira ta dauka muka gaisa ta na rawan baki. Ta kasa yi min mgana, sai ni ce na yi mata jajen mutuwar auranta. Cikin Sanyin murya tace"Hasiya ki yafemin, na gama dariyan taki kaddaran ga tawa ta fad'amin.". Kai Tsaye nace"Bakomai ni ban taba rike ki a raina ba." Batare da na tambayeta ba ta fara bani Labarin irin rashin mutumcin Da Sultana ta rika yi mata abun ba dadin ji. Ta karishe da cewa"Sai yanzu na gane a wannan Rayuwar da muke ciki in kaga kaddaran wani kada ka yi dariya Saboda baka san yadda taka zata zo maka ba." Nace kwarai da gaske,hakane Allah yasa mu fi karfin zukatanmu ya kuma zaunar damu lafiya. Mun jima muna hira da ita, ta na gayamin Yadda Sultana ta ci mutumcin su ta gudo nan Sajida tace"Wlh in ta yi miki wani iskanci ki ci ubanta." Ni dai dariya kawai na yi ban iya gayamata komai ba sai ma na kare sultanan nace muna zaune lafiya. Umma ma mun sake mgana itama na nuna mata muna zaune lafiya. Abunda ya ke bani mamaki da sultana  Mace ce Fitinanniyar mara son zaman lafiya. Duk hanyar da zata nemi fitina shi ta ke yinsa domin na tanka tamin Wulakanci, sai kuma ni ba na biye mata Tunda naga ko wanda ya Ijiyeta bata raga masa ba, ballata ni kuma saboda Tsabar rigima suna can suna ta karatu a makaranta ammh ita ba karatun ke gabanta ba. Neman Fitina dani da rashin son zaman lafiya. Shima na nuna masa tunda yasan Halinta ya daina biye mata, kuma ya daina mata mganar tafiya gaskiyanta ne itama ta na da iko da abunda ya ke mallakinsa ne. Kuma Assadiq na jin mganata in dai na bashi shawara ya na dauka kamar yadda nima na ke daukan na shi Shawaran Sai ga Sultana ta yi sati uku tare damu ta gama neman fitinarta taga bata samu abokin tafiya ba, dagani har shi mun koma mun saka mata na mujiya. Duk abunda tace shi ta ke so ayi zan Taushi Assadiq nace masa ya yi Hakuri don Allah mu rabu da ita lami lafiya. Ni fa har wake waken Habaici ta sha yi min na mai Farar kafa da bakar Annoba kala kala sunaye ta ke kirana da su har da bazawara mai kwacen miji. Ban taba daga kai ba, na sakata a layin marasa hankali da sanin Ciwon kansu wlh. Sai gashi da kanta tace ma Assadiq zata koma zasu fara Test a makaranta ammh suna gama Jarabawa zata zo nan ta yi Hutu. Ni kuma a raina nace Gusau zan je na yi hutu na in tagama Hutun ta dawo nima sai na dawo. Har Allah ka yi nisa da wanda baya kaunar ko ganinka. Saboda ita ya yi shirin tafiya Gusaubni kuma sai alokacin na gaya masa na yaye su Asim Ya fara min fad'a meyasa ban gayamsa ba nace zai hana ni, bai yi fad'an sosai ba saboda bai ga suna Rigima ba, ni ko abinci da kunu da tea na ke dora musu. Kuma suna girma suna kara Rage Rigimansu. Yace shikenan na Had'a musu kayansu Umma da Mama suna da manyan baki. Nima yaso na shirya muje nace masa a'a sai nan gaba gwara na zauna a gida na yi abunda na kudura a raina. A daran da zasu tafi na yi masa maganar kudurin da ke raina akan ina so na Rubuta Labarin Rayuwata da Tsaka mai wuyar da na shiga Saboda matsaloli irin nawa suna kara yawa acikin al'umma. Na dauko Sreenshoot din abubuwan da na Dauka saboda na nuna masa, na irin Labaran da suka yi kamaceceniya da nawa Labarin. Assadiq ya kalleni ina zaune a falo a gefensa Sultana ta shiga ciki bayan mun gama cin abinci. Cikin son karin bayani yace"Tunaninki tunani ne mai kyau My Siya, sai dai yanzu in kika ce zaki yi wannan Rubutun ta ina zaki fara? Ke fa ba marubuciya bace? Cikin kwarin gwiwan da na saka ma kaina nace"Zan nemi marubuta na yi shawara da su, ai ina tare da su ina karanta wasu daga cikin Littafan su. Ga Surayya Dee da muke mutumci da ita sosai Sanadinta ma nasan marubuta da dama dukkansu nasan in naje musu da mganata zasu saurareni kuma su bani shawara sannan ga Anty Habiba iman ikra tare da Anty Sumayyah Abdulkadir Takori  da kuma AuntySis tsoffin Marubutan bugawa ne tun Lokacin duniya na kwance, dukkansu ina da kyakyawan tabbacin in naje musu da kyakyawan niyyata zasu bani shawarwarin ta inda zan fara in sha Allahu." Cikin gamsuwa yace"Dakyau kuma duk wad'anda kika Lissafo duk marubutan ne? Cikin sauri nace"Eh Sosai ma, kuma suna yin Rubutu cikin ma'ana da Tsabtar alkalami." Assadiq yace"Shikenan bazan hanaki niyar alherin ba, tunda zaki Rubuta wannan Labarin ne saboda Mutane su gane ba mai yi sai Allah kuma Ubangiji bai isa ya yi ma bawa abunda Allah bai yi masa ba, In har goyon baya kike nema na baki dukkan Goyan bayana Siya ta." Cikin jin dadi nace"Nagode Mijin siya, ina kara nenan wata alfarma" Da sauri yace"Ina jinki fad'eta, in dai bata karfina ba zan yi miki " Da sauri nace"Ka min jagora ka zame min ido a kan wannan abunda zan yi." Hannuna ya rike kafin yace"In sha Allahu Matar Assadiq." Mun Cigaba da Tattaunawa ina bashi Labarai masu ban mamaki irin labaran da na ke samu a kan masu Fuskantar irin tozarcin da na Fuskanta a baya. Ya tambayani a littafi zan Fara Rubutun? Nace sai na yi mgana da d'aya daga cikin marubutan da na gayamasa shawaran da suka bani da shi zan yi amfani. Ammh ina so na wallafa wannan Labarin ya fita duniya in sha Allahu Mun jima muna mgana Sultana ce ta sake fitowa jinsa shuru ganin haka yasa na yi masa sallama na shiga ciki. Da safe tun asuba na tashi na shirya yara Naja ma na saka ta shirya. Weekend ne ranar Asabar daman tun jiya na yi miyar Naman rago sai na soya musu dambun kaji na zuba a roba nace a kaima Umma. Miya kuma na innani ne baiwar Allah, sai da naga zasu tafi naji dama na Bisu ammh kuma ina Bukatar natsuwa a gida. Sai da na Boye sannan suka samu tafiya da su Asim da ke ta kuka kayansu na had'a musu da yawa nace su sha hutunsu wajen kakaninsu. Sai azahar Assadiq ya kirani yace sun sauka, ina tambayansu Asim yana dariya yace Mama taja megidanta Umma ma haka. Innani na tambaya yace da sauki, bazai dawo ba sai an siya mata keken da zata rika zama akai tunda yanzu ta zama sai dai a kwantar kuma a tayar. Kafin Assadiq ya dawo na kira Surayya Dee mun yi mgana na gayamata kudurina taji dadi kuma ta bani goyan baya. Tare da wasu sharwarin, na kuma kira Hajiya Habiba iman itama sosai ta karbeni ta kuma ji bayanina ta kuma bani shawara. Na sake kira Auntysis saboda gogewarta a harkan Rubutu da Rayuwa gabadaya. Dukkansu sun bani shawaran na yi Rubutuna a waya saboda yanzu abun ya koma Direct Print in na yi sai a bugamin shi. Kuma bakinsu ya zama d'aya sunce bayan na buga zan iya sakin Labari a softy Copy yadda sakon da na ke so zai je ma al'umma da dama. Sun bani shawaran na yi Bincike sosai kuma na nemi mganar malamai da magabata. Ni kuma nasan ta wannan bangaren bani da matsala ina da Babban malamina a gefe wato Assadiq. Da ya dawo shi ya taikamin har na fara Rubutun a computer tunda ya siyamin wata na bama Habiba Tsohuwar tawa. Sannan Saboda ban saba ba Typing din ba, ya na bani wahala ammh hakanan Saboda na saka abun a raina yasa na Dage. Koda yaushe cikin bincike na ke yi, Assadiq na kara nuna min wasu abubuwan a Labarin Rayuwata nace bazan boye komai ba. Hatta sunanaye da garuruwan da abun ya faru saboda so na ke mutane su san cewa da gaske ne ba Farar Kafa a musulunci su kuma saki mganar mutane su kama Allah su gane Ubangiji ne ke da alhakin Faruwan komai. Ammh Assadiq yace ya na da kyau na sauya sunan garuruwa da wasu mutanen, ammh zan iya amfani da sunana tare da nashi sunan. Ya kawo min Hujja akwai wad'anda Labarin ya shafa kuma yanzu sun yi nesa da Rayuwata ambatan sunansu kan iya zama matsala ko anan gaba. Shiyasa sai na bi shawaransa na zan sauya garuruwa da sunayen wasu daga cikin su. Da na Fara na turashi zuwa wayata da Taimakon Assadiq na kuma Tutturama Marubutan da na yi shawara da su, su ka dubamin su ka kuma jinjina min sannan tare da nuna min inda ya kamata na gyara. Na saka abun acikin raina shiyasa bana jin nagaji. Kuma ga shi su Asim basa nan da na sallami Assadiq zan dukufa sai da ya fara min fad'a ne ma nake Tsayawa naci abinci, da sai yammah yini na ke yi da yunwa. Sannan da daddare ma nace sai nayi, shi ya ke hanani ya sakani dole na kwanta na Huta. Auntysis ce ta  fara ankarar dani ban sama ma labarin suna ba. Na yi ta Tunanin, wani suna zan sama masa ni da Assadiq mun fi kwana Biyu muna tunanin sunan da zamu saka ma Labarina. Sai da muka shafe sati sannan mu ka sama masa suna. Nace a iya rayuwata na Fuskanci Rayuwar TSAKA MAI WUYA.! Kuma na saka wasu Rayuwaka da Dama da suka Rab'eni acikin TSAKA MAI WUYA.! Shiyasa wannan Labarin nawa zan saka masa suna TSAKA MAI WUYA(LABARIN HASIYA). Assadiq yace tabbas sunan ya yi, suma da na tura musu sukace sunan ya hau da Labarin na cigaba da Rubutuna kawai. Kwarin gwiwan da na samu Daga duka bangarorin yasa na kara zake Damtse, kuma yan'uwana ba wanda ya sani Amma kad'ai na gayamata Tunda ita uwace. Ta kuma sakamin albarka acikin Lamarin, ni ba suna na ke so na yi ba, sannan ba sha'awar Rubutu ne a raina ba kawai dai ina son na Rubuta Labarina ne domin  masu Tunanin akwai mata masu Farar kafa su daina Da masu tunanin wani zai iya yi ma wani abunda Allah bai yi masa ba. Da masu Tunanin zawara ba mata ba ne sannan ba su da yanci da gatan da Sauran mata suke da shi. Wannan shine suka kara sakamin kaimi da Himma wajen Rubuta Labarina. Kwatsam ina cikin Rubutun karamin ciki ya Bulla a jikina Laulayi ya sakano gaba da dole na ijiye Rubutu a gabana na koma ina fama da kaina. Allah ya taimakeni sai da na yaye su Asim duk da ban ji dadin cikin alokacin ba ammh ban yi ma Ubangiji Butulci ba. Na tatattara Rubutun na ijiye a gefe ammh ba wai na hakura da kudurina ba ne. A cikin raina na saka ko shekara nawa zai daukeni kafin na gama zan yi kokarin na ga mashi in dai da rai da lafiya. Mata muntashi tsaye mu yaki infection (sanyi) Wani ciwone Mai nacin gaske Wanda idan kikayi wasa xaihanaki jindadin Aure Sannan maganin shi saikin daure da nacin shanshi Akai Akai toh kufito🤌🏽 KUSAI TSIMIN TABAJE DOMIN MUNA DAFASHINE DA INGANTATTUN SAIWOYI MASU AMFANI AJIKI DAKUMA LAFIYA, CIWON SANYI, SANYIN MARA, BASIR DASAURANSU INSHA ALLAH DUK WANI CIWO INDAE NA SANYINE ZAIZO KARSHE DA YARDAN ALLAH KIDAE KIDAURE KIDUNGA SIYAN TABAJE KIJEFI TSUNSTU GOMA DA DUTSE DAYA💃💃💃 Akwai infection Wanda yake nuna kanshi Akwai Kuma kurman infection Wanda baxaki San kinada shiba Amma yanacan yana Miki illa domin duk kyan Kayan mata baxakiga aikinsu ajikinki ba ko Kuma sumiki aiki bayanda akaso ba Anason duk bayan wata 1 mace tasha maganin infection sbd samun lafiyar jikinta Alamomin shi sune Fitar farin ruwa Kaikayin gaba/ko kuraje Jin zafi yayin sex Daukewar ni'ima Daukewar sha'awa dadai sauran su Kafin kifara Shan maganin mata yakamata ki fara Shan maganin infection Ina Yan mata Budurwa kema Yakamata kidinga Shan maganin infection Dan kariya da lfy ki karsai kinyi Aure infection ya Riga yamiki illa Baki saniba Allah y bamu lfy y karemu Ameen 🙏 *Janafty*  *TMWB3020* *TMW is a paid Novel, Pay 500 for regular or VIP N1K, Via 0552179550 Jamila Umar Gt bank, 09069067488* https://chat.whatsapp.com/K3rO5UonX4GDVxtQbA5mZl PAID ADVERT✅ Assalamualaikum wa rahmatullahi ta'ala wa barakatuhu!!! Wannan group din dai na komai da komai ne. A taiqaice *Farashin mu na daban ne compared to sauran Yan kasuwa *Kaya masu kyau da quality. Abinda kika zaba shi za a Baki * Swift delivery.watau waybill a sauqaqe da Yardar Allah * Muna sake New Arrivals ka fin su cika Gari * Muna iya duba maku kaya a good price ko da ba namu ba ne idan kuka Aiko da hoton kayan Allah sa mu qaru da juna Ameen Ashe bansan cikin su Asim kamar Bonus ba ne sai da na samu wannan, gabadaya na zama a rikice ba na iya komai laulayi na ke yi mai zafi ga Amai da miyau kamar na wanchan. Ga shi ba na son warin Tafasan abinci warin magi ma ba na so, ballatana na mai ko wani abu. Shiyasa na daina girki saboda in dai na shaki warin magi ko kamshin Tafasan girki in na rika Amai ranar kamar zan Amayar da Hanjin cikina. Mun je asibiti an gwada jinina duka duka cikin wattani biyu ne da wani abu, sau biyu muna zuwa ana sakamin Drip saboda karfin jiki sannan ba na iya cin abinci. Assadiq duk ya shiga damuwa Umma da taji cewa ta yi ya kawo mata ni Gusau har sai cikin ya yi kwari. Ni kuma sai naga kamar shawaran bata yi masa ba, sai na yi magana da Adda Fati nace ko Habiba ta turomin ita ta zauna tare dani. Ashe Habiban bata nan tana wajen Amma tunda suka gama Jarabawa. Sai Adda Rukayya ce da taji ana Jajen yadda za'ayi ta ce ga Amna ta nan zata iya yin komai ta gama primary bata riga ta shiga makaranta ba. Ban tab'a tunanin Babanta zai barta tazo wajena ba sai gashi ita Adda Rukayyan ta kirani da kanta ta na fad'amin Amna zata zo wajena ya za'a yi? Ina kwance Lokacin kamar Ruwa Assadiq ya tafi office, ga shi ma yanzu sun fara tafiye tafiye saboda aiyyukan Titunan da suke yi ana tura wasu daga cikinsu wajajen da suke ayyukan Tsoron Assadiq kada Tafiya ta fad'o har da shi, gashi ni kad'ai kuma bani da lafiya. Kullum acikin bargo na ke yini Saboda na rika rawan sanyi kenan, kai na kara jinjina ma iyayen mu mata Amma kuma kaunarta da Tausayinta sun kara ninkaya acikin Raina. Cikin Dakushewar murya nace"Adda Babanta kuma ya barta ta zo wajena? Ko baki gaya masa wajena zata zo ba ne? Cikin Sauri tace"Haba wlh ya sani na gayamasa, ai yanzu shima ya Fahimci duk canfi ne da mganar Mutane baki da wani matsala a tare da ke tunda yaga shaidar haka kina zaune gidam mijinki lafiya har kin fara gina kyakyawan Zuru'a." Cikin jinjina kai nace"Allah Sarki! Nagode sosai, yanzu to wazai kawo ta? Kuma kamar ta yi karama ku sakota a mota? Adda Rukayya tace"Babanta yace bazai yi gangancin Turata ita kadai ba, shiyasa na kira ki naji yadda za'a yi." Jin haka yasa nace ta bari Assadiq ya dawo in na fad'a masa nasan shi zai san yadda za'a yi. Haka ko akayi sai da ya dawo na gayamasa, shima sai da zamu kwanta Tunda in ya dawo aiki shi ya kan taimakamin na yi wanka sannan ya matsamin sai naci wani abu. Ina kwance a saman cinyarsa shi kuma yana aiki Bisa Computer dinsa da ke gefensa ni Tsabar yanayin da na ke ciki na manta da wani Rubutun da na fara jama'a ana ta kai waye zai yi na kaya. Kiran sunansa na yi ya amsa hankalinsa na kan abunda ya ke yi, ina fad'a masa ya kalleni kafin yace"Bansani ba gaskiya, ammh Tahir yace min za su zo shi da Amaryansa abunda za'ayu zan kirasa na tabbatar shin yaushe zai taho? In cikin sati nan ne sai nace don Allah ya Biya ta Zariya ya Daukota tunda yace min a ranar da za su taho sai ya shiga kaduna." Da shawaransa muka Tsaya a daran ma yaso ya kirasa na hanashi. Cikin daure fuska yace"To uban me ya ke yi yanzu? In amarci ne ai ya gama cinye romon tuntuni." Ina Mirmishin karfin Hali nace"Kada dai ka kirasa, in har kai da ka ke da ni baka gama shanye Romon ba, shima mai auren jiya jiya ai bai gama Cinye Romon ba" Yana yar Dariya yace"Ina ta ko shan Romo na mai d'an karen dad'i. Ga shi nan sakamakon Romon ne ya nuna a jikin ki.". Ya karishe fad'a ya na shafa jikina ni kuma na Ture hannunsa na sauke kaina a saman cinyarsa na maida saman Filo cikin Bushewar baki nace"Assadiq sai da Safe." Saboda bakina yanzu sai ya rika Bushewa har yana fashewa ni dai wannan cikin naga Jalala kala kala. Sai washegari da Safe ya kira Tahir ya na tambayansa yaushe zai shigo.? Shi kuma yace abunda zai kaisa kaduna an daga sai wani sati. Da Assadiq ya gayamin sai nace zan kira Adda Rukayya na gayamata Amna ta shirya sai ta jira Tahir din Sati mai zuwa ya biya ya Daukota. Haka muka yi dole tunda ba wanda zai Taho da ita, Assadiq ya gayama tahir yace ba matsala ta zo gidan Adda Fati tunda yasan gidan sai ya Biya ya Daukota. Yanzu tsakanina da Tahir sai gaisuwan mutumci da girmamawa Sannan zumunci na ke yi da Hauwa'u sosai kamar mun zama yan'uwa. Allah ya taimake ni a satin Safiya ta kirani tace ta raka Mamansu Abuja bikin diyar kanwarta sun kawo Amarya nan cikin garin Abuja. Tace ta na so tazo sai naji dad'i daman tasan bani da lafiya nan ta ke na Tura mata Address ba dad'ewa sai gata. Ta yi jimamin halin da ta ganni, duk na tsumaye na rame kamar ba ni ba sai Farin Fata da ido. Gabadaya kananun jikina sun kara bayyana daman can a baya gyaran jikin na kama sannan kuma cikin ma ba d'aya ba ne da na su Asim Wanna daga gani in ban yi wasa ba kafin ya girma sai na zama abun Tsoro. Ita da ta zo min bakunta itace ta Tube ta zage ta gyaramin gidana tas ciki da waje, Assadiq baya samun Lokaci sai Weekend wannan karshen watan ma saboda ni bai tafi Gusau ba. Ina ji suna waya da Sultana ta na kananun mganganunta da ta saba. Ya fad'a mata ina da Ciki kuma ya na wahalar dani zai tsaya ya kula da ni. Nasan dai Sultana na can bakin ciki kamar ya kasheta. Ta so ta tafi a ranar tunda tace gobe da Safe zasu koma Zariya ni na Hanata tafiya tunda ta kai Dare, har girki sai da ta yi min ta kuma matsamin na yi wanka. Ni daman ban iya cin komai sai Farar shinkafa ba mai ba manja ba maggi Hakanan na ke iya turawa in naji kamshin mai ko magi wlh ranar bazan kwana Lafiya ba. Shiyasa da ta yi mai miya ni sai naci fara hakanan da Assadiq ya dawo shi kanshi yaji dadin ganin gidan da ni kaina. Allah Sarki har ya Biya ya siyo abinci ni kuma ban yi hausan na kirasa nace kada ya siyo wani abu ba. Sai fad'i ya ke yi"Safiya kin zo mana Bakunta muna ta saka ki wahala." Kai Tsaye tace"Ni ai ba bakuwa bace ni yar gida ce, kuma lalura ce fa." Ina gefen mijina nace"Tun da ta zo bata zauna ba, sai aikace aikace ta ke yi da na yi mgana sai tace ita ba bakuwa ba ce." Assadiq yace"Gaskiya ne mun gode sosai Allah ya bar zumumci." Ranar dai bata tafi ba sai da safe suka fita tare da Assadiq zai kaita kafin ya shiga Office. Sai naji kamar kada ta tafi ammh ba Dama tunda mamansu na ta kiranta za su tafi da wuri, jin ma ba ni da lafiya ne yasa ta barta ta kwana kuma Safiyan ta bani ita mun gaisa ta yi min sannu. Na gayama Amma bani da lafiya ammh ban gayamata ciki gareni ba, ita da kanta ta gane sannan sun yi mgana da Adda Fati ita ta gayamata zencen zuwan Amna wajena. Amma ta kirani ta na cewa"Ko dai Habiba tazo wajen ki ne, ni nan ba wani abunda ta ke yi min naga zata fi Amna amfani tunda ta fita shekaru." Ni kuma ganin Habiba bata taba zuwa ta jima wajen Amma ba yasa nace ta kyaleta kawai ai ba wani abun wahala ba ne Tunda Adda Rukayya ta bani Tabbacin Amna zata yi min komai in dai ba mai wahala ba ne. Sai Amma tace shikenan Allah ya kara lafiya. Kafin mu yi sallama sai da tace"Ina Mazajen nawa? Ba sa cefane kuma ba sa zuwa zence? Ina dariya nace"Amma suna gusau ba su dawo ba." Amma tace"Kin huta da yanzu ai aikin ya yi miki yawa" Kai tsaye nace"Ai nace su yi zamansu can sai na warke Amma bazan iya ba ji na ke yi kamar zan mutu." Amma tace"Ki bar cewa Haka Haseta. Haka kowani ciki ya ke da na shi Tarnakin Allah dai ya sauwake ya kuma Raba lafiya." Sai naji kunya amsar ma a sannu na amsa ta. Mun gama waya da Amma kenan sai ga kiran Umma itama muka gaisa ta gaisheni tunda ko jiya ta kirani ta gaisheni da jiki. Ni da kaina na ke gayamata diyar yayata zata zo ta taimakamin Umma tace"Eh gwara haka ko ya ya mutum ya ke ai Rahama ne. tunda ga su Asim a wajena." Cikin karfin hali nace"Umma su sha zamansu wlh, in suka dawo bazan iya da su ba." Umma na dariya tace"Jiya ai sun yini Hiran Mami, Jiya Asif da rigima ya tshi ashe zazzabi ke jikinsa sai da na bashi mgani" Sai na ke gayama Umma su Asim ba su cika yawan ciwo ba sai dai ko zawon Hakora da suka yi ta fama da shi Shima din bai ba su wahala sosai ba. Kaf yayayen Assadiq ba wacce bata kirani ta yi min sannu ba, Hatta Sadiya itama ta kirani ta min sannu Sajida kuma daman tunda muka daidaita lokaci bayan Lokaci muna mgana. Allah sarki har ce min ta yi in ina so sai ta yi ma Umma mgana ta zo ta taikamin, ni kuma kunya da nauyi suka saka nace ta yi zamanta bakomai. Bazan iya kwanciya yayar mijina na Hidima dani ba abun akwai wani iri aciki. Da na gayama Assadiq ma a lokacin Dariya kawai ya yi kafin yace"Ikon Allah Su Sajida an zama gama garin zawarawa." A lokacin da ya fad'i haka sai da nace"To wai bazaku iya gyara Lamarin ba Assadiq? Assadiq yace"Abba ya zauna da shi, laifin fa duk na Sajida ne ko za'a gyara sai in shi mijin ne ya dawo yace zai maidata kuma abu ne da ya had'a da Uwa dole kuma ya yi ma mahaifiyarsa Biyayya, ni tausayinta na ke ji ya'yanta Uban duk ya rabata da su Yar kibar nan ta Sajida duk ta ta fi, bakin nan nata da baya shuru da Had'e had'e rayuwa ta gama nuna mata gaskiyan da ake gayamata bata Dauka ba, duk ta zama wata a firgice." Ya na wannan mganar ina Hasaso abunda ya faru dani Lokacin da Abubakar ya sakeni. Kusan zauncewa na kusa yi, na fita Hayyacina kai Allah ka raba kowata mace da kaddaran sakin aure da zawarci. Kamar yadda muka Tsara Tahir ya Biya ta Zariya ranar Wata alhamis ya Taho min da Amna. Da ya ke wani Taron siyasa ya karfafa ma Tahir shigowa Abuja kuma daman Hauwa'u ta matsa zata Biyosa ta zo wurina yasa ya zo da ita. Sanda suka iso Assadiq na wajen aiki shima yana sauke su ya wuce inda zaa shi. Dakin da Sultana ta sauka na sauke Amna da Hauwa'u. Hakuri na ba ma Hauwa'u na Roketa ta shiga kitchen ta da fa musu wani abu su ci ni dai ba na iya moran kaina Ballatana na Morama wani. Hauwa'u tace"Haba bakomai bari na shiga na girka" Da ta tambayeni me zata girka nace abunda zai fi sauki tunda tafiya suka sha. Ni kuma na shige daki na kulle kaina saboda kamshin girki in na shaka ba zaman lafiya. Ina da sauran miya tun wanda Safiya ta yi ne kafin ta tafi, Sai ta dafa musu Taliya fara suka ci da miya. Ni kuma na Tura gaya hakanan na sha Ruwa. Amna kuma ta shiga kitchen ta na wanke wanke, Adda Rukayya ba ta wasa sosai ta ke koyama ya'yanta ayuukan gida saboda Rayuwa. Muna falo ni da Hauwa'u muna ta Hira, ta na gayamin taji dadin kayan gyaran da ta siya hannun Surayya Dee. Ni na had'a su tunda na gayamata ingancin kayan tace taji dad'in mganin sanyin nan tare da tsumin nan, ita yanzu kazar Amare ta ke so ta kara siya taci. Ina daga zaune nace"Ki siya wlh kazarta na da kyau, kuma ta na jimawa a jikin mace ta na aiki, nima fa na so na kara siya sai kuma ga Laulayi da gudu na watsar da su na yi ta kaina." Hauwa'u na min dariya tace"Result din gyara ne kika gani fa Madam" Ina jin miyau ya Taru a bakina nace"Uhm ai naga gyara sosai." Ni na gayamata Surayya ta fara Dahuwar Tatattabaru sosai kuma suke da inganci nan take Hauwa'u tace zata yi mata mgana ta na so. +234 803 277 3332. Ina raina Amna sai ga ta, ta zage ta share min gida tas ta goge ta saka Turare. Ko da ya ke yanzu shekaranta sha uku, ta riga Adda Fati haihuwa ita Adda Fati ta jima ba ta Haihu ba ne sai Adda Rukayya ta dauke girman. Hauwa'u kuma ta yi musu abincin Dare har da mazajen namu. Ni nace ta yi girki saboda su kada su dawo ba abinci. To ba su shigo da wuri ba ma, cikin su ban san wanda ya tsaya wajen d'aya ba. A tare dai suka shigo gidan suna Hiransu suna Dariya, Hauwa'u ce ta shirya musu abincin ta kawo musu Amna ana sallar isha'i ta yi barci. Ni kuma saboda kamshin abinci ina daki amma ina jiyo maganganun su tunda ba sa mgana a hankali kamar mu. Ina ji Tahir na yi ma Assadiq tsiya da cewa yace kawai kuku ya kawo musu daga zuwan matarsa ta zama mai yi masa girki shi da matarsa. Shi kuma yace masa ai shima an taimakesa yadda ya ke jin yunwar nan in bai samu abincin nan ba ai akwai matsala sannan ga Musulunci akwai taimakon dan'uwa musulmi wannan shima ya yi jihadi ne. Ina jinsu suna ta cacar juna kamar yadda suka saba Tahir na ce ma Assadiq ya shiga uku da Jaraba,  yana da kananun shekaru kafin ya yi Hamsin ya kai ga ya'ya ashirin Kilama yanzu haka Sultana ciki gareta. Amsar da Assadiq ya ba ma Tahir ce ta bani dariya. Wai ai ni ka shaida lafiyata kai ne dai na ke tunanin ko dai ko dai da matsala ne!? Sai ga Hauwa'u da gudu ta shigo daki tana fad'in"Abokan nan ba sa jin kunyar fad'in mgana mai nauyi." Ina kwance nace"In dai Assadiq ne ba'a kada shi a mgana, shi kuma mijin ki tsokana da neman zence." Dole ai ta bar musu falon ta dawo wajena muna ta Hira. Tana fad'in tsoro ta ke ji ta samu ciki Tunda ta na karatu. Ni kuma nace mata abun na Allah ne ta yi fatan Allah ya zaba mata mafi alheri. Sai wajen sha d'aya na dare Assadiq ya leko yace Hauwa'u ta shirya Tahir yace ba zai iya kwana shi kad'ai ba. Ina daga kwance sai da na mike cikin mamaki kafin nace"To ba ga dakuna ba, sai ku kwana tare." Assadiq yace"Haka nace masa, ammh sai naga yana nokewa." Ni ko kamar da sauri nace"To don Allah Assadiq ka roke sa mana." Asaadiq yace"Ke kam da son jan zence ki ke yi, kika sani ko yana Ihun dare ba ya so mu ji? Hauwa'u dauko mayafiki dare ya yi." Hauwa'u kunya ya hanata Dago kai sai ta mike tana fad'in" Kayana na can dakin." Assadiq ya bata hanya ta fita sai ya kariso gareni ya zauna kusa da ni. Lokaci d'aya yaga na hade rai sai ya yi dariya kafin yace"Da safe za su dawo kada ki damu kin ji ko my siya? Ina zumbura baki nace"To me yasa bazasu kwana anan ba? Hancina ya ja kafin yace"To na gayamiki kada ki matsa, kinsan akwai mazan da ba sa iya sarrafa jin dad'insu kila yana cikin su ne, kinga kuwa da kunya aji ihunsa a gidan abokinsa kuma yadda Tahir ya ke sabon shiga a lamarin kinsan ba'a daga kafa kullun ne Til Down." Hannu na saka na dokesa a cinyarsa sai ya sosa wajen yana dariya kafin yace"Me kuma na yi? Ina hararansa nace"Bansani ba, Assadiq ihu fa? Wani irin Ihu kuma? Assadiq na dariya ya sunkuyo ya na min Rad'a da yasa na fara Turesa ina fad'in"Assadiq..Assadiq.." Hannayena ya rike duka Biyu ya sama min karfi yana fad'in"Irin wannan irin wannan da ki ke sakani? Ko na gwada miki irin shi ne? Ai sai na yi lakwas ina kallonsa cikin ido kafin nace"Ka yi wa girman Allah ka yi shuru." A kunne ya k'aramin Rad'a abunda ya aikata yasa sai da na koma na cukwikwayosa ina jin kunya Lokaci d'aya da Dariya. Shi ma yana tayani har yana matsenin hanci yana fad'in"Ke siya kunyar taki ba ta fulani ba ne ko? Ina Make kafarsa da kafata nace"Ta zamfarawa ne ko? Baki ya Bude kafin yace"Bangane ba! Allah yasa ba mgana kika maida min ba." Yadda ya Tsaya ya na kallona ne yasa na Fashe da dariya, shima kuma sai ya Tsaya ya na kallona lokaci d'aya yana girgiza kai kafin yace"Lalle Siya. to nagode." Gabadaya mun Shagala mun manta da su Hauwa'u sai can ya tuna ya  tashi da sauri ya fita Falo wayam. Sai ga shi ya dawo ya na ce min"Tahir fa tuni ya tasa matarsa sun tafi, falo sai wayam ba kowa." Kai Tsaye nace"bazai tafi ba, ka zaunar da shi ka na yi masa sharri." Yana Tube rigarsa yace"Gaskiya na fad'a, bari na yi wanka." Sai da ya fito ya tuna da bai ga Amna ba da sauri yace"Ina d'iyarki ne, ban ganta ba? Ina kara shigewa cikin Bargo nace"Ta na dakin can, ta yi barci tun dazu." Cikin jinjina kai yace"Amma dai taci abinci ko? Sai na gyada masa kai lokacin Miyau ya cika bakina sai da na tashi dakyar na shiga Tiolet na zubar. Na fito ina numfarfashi Assadiq ya kalleni yana fad'in"To ke ki samu wani Roba ki rika tara miyan aciki mana, zaki gaji da zirgan zirgan ta shi kuma" Ina zama gefen gado nace"Ba ka jin kyamata ne? Hararana ya yi kafin yace"Kyamar me? Ni da na yi sanadin miyan." Ya fad'a ya na karisowa kusa dani, Dagashi sai karamin wando duk sanda zanga Assadiq a haka ba na iya had'a ido da shi. Sai na juyar da kai zan kwanta ina Fad'in"Baka jin sanyi ne wai? Saurin Taro kaina ya yi yana so sai na kallesa naki, runtse idanuwana na yi ina kiran sunansa cikin Shagwaba. "ASSADIQ.." Da tafukan hannunsa duka ya saka ya Taro fuskata cikin wani yanayi yace"Meyssa bakya iya kallona a suffata ta Namiji? Shuru na yi masa, kuma na kasa kallon nasa sai ya ce"To Allah yau sai kin kalleni, ji min yarinyar nan." Sai ya fara min sosa a wuya kamar tafiyar tsutsa na fara zillewa ina Dariya. Duk bai ishesa ba sai da ya fara min cakulkuli a ciki dariya na ke yi kamar zan shid'e ina kiran sunansa ammh bayaji sai cewa ya ke sai na kallesa." Da sauri nace"To to ka tsaya naji zan kalleka." Cikin Sauri yace"Kin tabbata? Ina haki da Numfarfashi na Daga masa kaina sai ya kyaleni. Numfashi na sauke kamar zan dago na kallesa sai kawai na yi saurin Kwanciya na ja bargo na Rufe kaina ina Dariya. Shi kuma dariya ya yi kafin yace"Siya yanzu ke sai ki yarda zaki iya yi min wayau? Bi na ya yi ya danne ya tura kansa Cikin Bargo duk da ina faman Turesa ammh ko gizau. Cikin rad'a yace"Tunda kika sab'a mgana ga Hukuncin ki." Na Bude baki zan yi mgana naci ya kame bakina ya had'a da nashi. Da zafi zafi ya ke yi ma bakina Hukunci sannan kuma ya kama Hannayena ya rike su gam da ba na iya wani motsi. Dole dai na saki jikina, na mika masa Ragamar Rayuwata gabadaya a hannunsa. Da asuba na kasa tashi duk jikina Tsami ya ke yi min, nasan ko irin Hukuncin Assadiq. Yana gani ina tafiya dakyar yana min Dariya bayan ya dawo sallar asuba. Ni kuma na yi masa Fuska na kumbura Fuska har na Dauro alwala nazo na yi sallah. Bayan na idar kuma na zo na kwanta a can gefe na juya masa baya shi kuma yana duba wani abu a wayarsa. Sai ga shi har ta bayana yazo ya na Leka Fuskata. Harara na maka masa ina kara Hura Hanci. Sai kawai ya duka ya sumbaci Goshina kafin yace"I love u My siya. Allah ya yi miki albarka." Sai naji zuciyata ta yi haske cikin mirmishin jin dad'i nace"Ameen Assadiq mijin Hasiya." Ina kwance ina jinsa sanda ya yi wanka, sai da ya fito ne yana Shiryawa na lallaba na fita abun mamaki a kitchen naga Amna har ta saka Ruwan zafi a Butar da na ke Dafawa. Ta na ta goge goge a kitchen din, tana ganina ta yi saurin gaisheni na amsa ina fadin"Eyee Amna an girma, to me zaki dafa muku? Kin iya soya kwai? Ta gyad'amin kai, ammh kada na barta ita kad'ai yasa na tsaya ina gayamata abunda zata yi. Nace ta saka kayan kamshi da albasa saboda karni. Falo na koma na Tusho hancina da Hijabi ammh kamshin kwan har ya Fara sakamin tashin zuciya. Assadiq ya fito cikin Shirin fita yana ganina na toshe hanci yace"Siya to haka zaki cigaba da zama baki son kamshin komai? Shima yana mgana ina jin kamshin Sabulan wankansa  tunda na hanashi saka Turare na kwashe gabadaya na boye. Kamshi daya na ke shaka na zauna lafiya shine na Turaren wuta. Ganin ina yunkurin Amai yasa na tashi da gudu na koma daki na kwanta ina toshe kaina acikin Filo. Ko da Assadiq ya gama karyawa ya zo min sallama na yi barci. Nima zuwan Hauwa'u ya tadani na tashi na iske Amna ta gyara gidan tas yana tashin kamshi. Kafin Hauwa'u su koma ita ke yi abincin dare saboda su Assadiq, ammh duka duka kwana Hudu suka yi suka tafi. Ban so tafiyar ta ba ina ta ce ma Assadiq ya roki Tahir ya bar ta su yi ko da sati. Yana kallona yace"Siya ke fa wani lokacin kina da rigima, mutum da matarsa kuma sai kice ya tafi ya bar miki ita anan? Da sauri nace"A'a ya zauna shima ya yi sati mana" Dariya ya fashemin da shi da ya harzukani na juya masa baya. Ya yi saurin Rumgumeni ta baya yana Fad'in"Tahir fa yana da abubuwan yi Siya, sai ya zo kawai ya tare a wajen mu? Sorry kin ji to ki bari in kin Hauhi sai mu je wajensu  mu yi musu wata d'aya tunda baki son Rabuwa da Hauwa'un" Yadda ya fad'i mganar me yasa nasan zolayata ya ke yi, Bayan hannuna na saka na Tokare masa kirji. Shi kuma da yaji zafi sai ya matsemin Nono na guda d'aya. Da naji zafi na make hannunsa ina Fad'in"Assadiq makasata ne fa?. Yana dariya yace"To ke ma ki rama a nawa makasan mana? Ya fad'a yana kashemin ido d'aya. Kallonsa na yi bakina alaikun naja jikina na sauka daga gadon ina fad'in"A'a ba sai na rama ba, na yafe maka Assadiq." Kokarin tashi ya ke yi ya Biyo ni na zura da gudu ya kira sunana yana fad'in"Siya ki yi a hankali." Haka muka cigaba gudanar da Rayuwarmu ni da Assadiq cikin rayuwar da muka zab'a ma kanmu. Ba zan ce  ban taba ganin ma'aurata kamar mu ba, ammh dai za'a dade ba'a samu kamar mu ba. Ba wai bama samun sabani ne bane muna samu, ammh kuma muna kokarin daidaita kanmu. Tunda musan hallayan junan mu sai muka ci mganin zama tare. Tausayin junan mu shi ya fara gina zaman aurren mu, sannan daga baya soyayya da kauna suka Biyo baya. Sannan ni kuma na zauna da shi Cikin Biyayya, Duk abunda na san zai sab'a ma Assadiq ina kauce masa shima duk abunda yasan zai sosa min rai yana kauce ma aikata shi Saboda kada raina ya so su. Zuwan Amna ya taimakamin sosai ta iya saukakkun girkr girke, Har Assadiq shima mamakin kokarin yarinyar yake yi har ni sai da ya yi min mgana. Da safe ita zata dafa musu abun karyawa kamar su tea, soya kwai ko doya ko dankali. Da rana kuma nace ta dafa abunda ta ke so, in kuma wani abu zata sha ko goldemorn ko Cornfl sai ta jika ta sha, da Daddare kuma na kan nuna mata abunda zata yi ko ta Dafa shinkafa jalop ko taliya. Sai dai ina gefe na toshe hanci watarana na wanye lafiya watarana kuma na yi ta kwarara amai. Assadiq kan siyo Tuwo watarana da daddare in yaji sha'awan haka. Wannan watan ganin Amna yasa yace zai je gusau ya Duba Sultana da su Umma nace yakamata. Ranar jumma'a ya tafi da safe ya barni dagani sai Amna. Ni fa kwanciya ce aikina kamar wata mai laluran barin jiki. Wayar ma yanzu in ba kirana aka yi ba, bana bi ta kanta. Kwana Uku Assadiq ya yi ya dawo ya kawomin Hotunan su Asim da Viedo da ya yi ta daukansu. Sai suka karamin girma a ido, yace ko damuwa ba su yi sun zama yan gida. Har Innani sai da tace ya'yan  magajin gida sun zo da alheri gidan nan. D'an zagayen da suke yi a bangarenta tace yana deb'e mata kewa sosai. Kuma yace da zai tafi ba su yi kuka ba har suna yi masa Bye bye. Umma na cewa ba za su ku je wajen Mami ba? Suka noke a jikinta. Ina dariya nace"Shikenan sai mu bar ma su Umma, mu ma zamu haifi namu Allah ya bani yar mace ina so Assadiq." Yana kallon Wayarsa yace"Allah ya baki, mafi alheri siya." Na amsa masa da Ameen. Sai washegari da bai fita aiki ba baya jin dadi zazzabi ya kwana da shi. Sai nace ya kwanta a gida ya huta sai dai ya kira can  wajen aikin su ya gayamusu. Dani da shi ranar a daki muka yini, muna shan soyayyarmu da Hiran mu. Muna kwance ya bani wayarsa ina kallon Hotona sai naa ga Ummi an Dauketa ta yi kiba kamar ba ita ba. Sai na juya ina kallonsa ya na kwance ya Rufe ido ammh ba barci ya ke yi ba. Tab'osa na yi kafin nace"Na manta ban tambayeka ba ya su sultana da Ummi? Fata suna lafiya? Assadiq ya yi shuru kafin can ya mike zaune da sauri yana dariya. Cikin mamaki nace"Miya faru? Cikin gyad'a kai yace"Sultana na can na kuka wai na yi sonkai na kara yi miki ciki ita ban yi mata ba." Ido na zaro ina kallonsa shi kuma sai ya yi dariya kafin ya cigaba da fad'in"Wlh rigimar da naje tarar ta na yi kenan, tace ba na mata adalci ina Fitita ki a kanta, da farko cikin yan Biyu na yi miki ita kuma da ba na kaunarta d'aya na yi mata shine yanzu da son kai da rashin Adalci na yi miki Ciki ita ban yi mata ba to wlh itama bata yarda ba in ina son na zama mai adalci itama na yi mata ciki." A tare da ni da shi muka Fashe da dariya cikin Dariya nace"Assadiq to kai baka yi adalci ba, me yasa ka dawo ba ka yi mata cikin ba? Mirmishi ya yi kafin ya koma ya kwanta ya yi filo da hannayensa. Cikin Tattausan lazafi ya kira sunana"Hasiya." Na amsa masa sai ya mika Hannun ni kuma na kama ya jawoni jikinsa ya Rumgumeni na yi matashin kaina a saman kirjinsa. Cikin Sanyin murya yace"Ina so na fad'a miki wata magana." Cikin ba shi hankalina nace"Ina jinka. Sai ka fad'a" Kai Tsaye yace"Kin san meyasa na gayamiki wani abu daya danganci sultana game da ni yanzu? Sai na girgiza masa kai, yana shafa kaina yace"Saboda na nuna miki Sultana bazata taba sauyawa ba. Halinta ne haka zafin kishi zargi da kuma rashin son zaman lafiya, a baya  na damu da Fitinarta ammh daga baya da na zauna ma Fahimci halinta har ga Allah lamarinta ya Daina damuna, can u just imaging ta tasani gaba ta na min kuka wai sai na yi mata ciki in ina so na yi adalci.? Ina yar dariya nace"To sai ka ce mata mene? Ajiyar zuciya ya sauke kafin yace"Me zan ce mata? Tun ta na bani mamaki sai ta dawo bani dariya da Tausayi, yanzu dai na lallasheta nace ta bari itama zan yi mata ciki tunda shi ta ke so" Mirmishi na yi ban yi mgana ba shi kuma ya Cigaba da fad'in"Shiyasa na ke son na gayamiki ki yi hakuri da ita don Allah kin ji ko? Tunda mun san halinta mu zauna da ita a yadda ta ke" Ina jinsa sai na gyad'a masa kai ina fad'in"Baka da matsala dani in sha Allahu" Da bakinsa ya ke fad'amin wasu daga cikin Rigigiman su, wasu na yi ta Dariya sultana yar bala'i ce wlh. Yace yanzu duk ta b'ata da su Sadiya aammh yasa ta ba su Hakuri. Yace Har Umma fa in abunta ya tashi sai ta yi mata yaji tace an yi mata gori ko Umma ma nuna son kai. Yanzu ma zuwan su Asim sai da tace Umma ta yi sonkai. To itama Ummi zata kawo mata, Umma tace sai ta bari ta yayeta. Ammh sultana bata ji ba sai ga shi ta had'o kayan Ummi ta kawo ta wajen Umma. Ina Dariya nace"Kai to wannan jaririyar aka rabata da uwarta ai sai a dauki hakki." Assadiq yace"Umma tace Shegantakan Sultana ya isheta wlh, sai da Abba ya shiga mganar yana ta lallashi yanzu dai tace itama ta na yayeta Umma zata riketa Tunda ta rike ya'yan kishiyarta." Yana bani Labarin ina auna wasu abubuwan. Nan take na kara tabbatar ma da kaina Sultana bazata tab'a sona ba. Sannan ko kwanta mata na ke yi bazata bar kishi da ni da gasa dani ba. Na fahimci duk wani abu da zata ganni da shi sai ta yi kokarin mallakan wanda ya fishi a Tunaninta ta fini, sannan ta na ganin Assadiq ya fi sona shiyasa ya ke nuna mata rashin adalci. Alhalin adalci daidai gwargwado yana yi mata kishinta da Zarginta da Rashin mutumcinta yasa ta kasa gane komai. Tundaga Lokacin na fahimci ita Rayuwa ba ta cika 100% bisa dari  in kaji dad'i a wani bangaren Dole ta wani bangaren asamu akasin haka. Sai ka yi hakuri da yadda taka Rayuwar ta zo, haka kila kafi wasu wasu ma sun fika. Cikin ikon Allah na Cigaba da Renon cikina Amna wajen wata uku ta yi min sannan ta koma gida tunda za ta shiga makaranta. Saboda nuna godiya da ni da Assadiq muka maidata har gida tare da shatara na arzikin da Assadiq ya yi mata. Mun yi mata sabbin d'inkuna kayan kwalliya littafan makaranta da jaka da takalma Assadiq har karaman Ipad ya siya mata saboda karatu. Adda Rukayya na ta godiya da Mijinta Adamu dai kamar ba shi ba. Ya zauna da Mijina suna ta Hira har yana kallona yace"Ikon Allah Hasiya ki yi hakuri da abubuwan da na rika aikata miki a baya, wlh sai daga baya na kara gane cewa duk zencen mutane ne, sannan naji wani wa'azin kwanaki da akace rashin yarda da Allah nw in wani ya samu bawa yana nuna mutum bai yarda da musulunci da ya ke ciki ba kenan." Assadiq yace"Kwarai ma da gaske, ai acikin shikan shikan musulunci akwai yarda da kaddara mummuna ko kyakyawa." Sai ga shi zamu tafi Amna na hawaye nima wlh na saba da yarinya mai kwazo ga hankali. Assadiq yace ta bar kuka duk sanda ta samu hutu zai rika zuwa yana Daukanta. A gidan mu na zariya muka sauka da ya sha kura, Allh sarki maman suhailat sun tashi d anta ya gina gida sun koma can wajen kabama. Ummi ma sun tashi gidan duk bakin Fuskoki ne. Dakin ma Assadiq yace zai sake shi, sai dai in ya samu kudi ko karamin gida ne ya gina mana in da zamu rika sauka in mun zo garin. Wannan zuwan da muka yi Amma ta matsamin sai na ne gidan Baba Tanko tare da Assadiq muka je  har gidan Baba Saminu. Sannan na kaisa gidan Goggon kona itama suka gaisa sai kuma jin kunya, suna ta kame kame a raina nace ku kuka sani ta bakin Amma tace mu mun riga mun sauke hakkin zumumcin da ke kanmu. Kuma Assadiq ya yi musu alheri suna ta Tambayan yan biyu nace suna Gusau. Hatta wasu daga cikin yayansu masu zagina da mugun baki na gansu, sai kunya da sunne kai. Mugun abun da suka Rika jefani da shi ya koma musu. Tunda cikin ya'yan Baba Tanko akwai sakakkiya auranta uku baya zama ta na gida, nidai nace alhakina ne ya kamasa da ya rikamin mugun baki in ma na yi aure bazan zauna ba Tunda na zama bakar Annoba gobara daga kogi mganinta sai Allah ba. Daga zariya ne muka je Gusau nan  muka yi jima Tunda Lokacin hutun karshen shekara ne. Su Asim sun zama yan gusau ina wuri ma kamar ba na nan Umma da Mama ne iyayensu yanzu. Muna garin Siyama ta haihu har aka yi shagalin suna. A sunan ne su Anty Sakeena  ta yi ma Sajida tsiya lokacin da bazawarinta ya kirata a waya. Sai a lokacin naji ashe wani Tsohon saurayinta da ya nemeta tun tana Budurwa ne ya Dawo kuma abun mamaki bai yi aure ba shi har yanzu. Saleema ta zo sunan itama da Cikinta Tunda sau biyu ta na samun b'ari. Ita kuma asibiti ta ke zuwa Tunda in dai ta samu ciki sai ya zube. Duk ta rame ta zub'e ba wannan gayun sai a hankali. Shahida ke bada labari a wajen suna irin yadda Baba Jibril ya rika nuna ko Salimar ne ke da wani Laluran a jikinta? Kamar ya na nuna shi fa matsalan daga wajen salima ne ya manta Allah ke kashewa da Rayawa. To ina Baba Jibril yasan Allah shi ban da neman duniya ai bai saka ma komai gaba ba. Don ma Saboda Abba ne yana karuwa ta bangarensa da Tuni salima ta wulakanta kuma domin mijinta na sonta. Ammh in akace Salima ta yi b'ari suna asibiti ji ya ke yi kamar kud'insa ne za su yi kuka ya yi ta mganganun rashin Takwalli. Ni tausayi ta bani, ina auna irin yadda Rayuwar mata ke fuskata a wannan zamanin Allah dai yasa mu dace Ya kuma cika zuciyoyin mu da Takwalli da yakana. Wannan karon a Abuja na Haihu ammh kuma a Gusau aka yi taron suna. Kuma na haihu da kaina batare da an sake Farkani ba Ban samu macen da na dinga kwad'ayi ba namiji na kara haifa. Assadiq kuma ya saka masa suna TAHIR.! Tahir ya yi murna Farincikin da ya Hauwa'u ta yi min sati a Gusau ta kuma zo min da kayan arziki daga Takwaransa Tahir Yusuf Daura. Tahir da ya zo barka ya Dauki takwaransa ya rike cikin Farinciki yace"Abokina me na yi maka da na Cancanci ka Tsallake sunayen mutanen da suka fi daraja ka saka ma d'anka sunana? Kai tsaye Assadiq yace"Da taimakon ka na auri Siya, Tahir ka yi min komai da  bani da bakin da zan gode maka." Tahir kamar ya yi kuka yace"Me na yi maka! Ni da na rika adawa da auran ina ta cewa baku dace da juna ba, ashe muna namu Allah ya gama nashi ashe ashe har Takwara ma yar Zabiyar matarka zata Haifa min Nagode kwarai Allah ya raya Junior Tahir yasa ya Biyo mai halinsa." Assadiq na jijjjiga kafad'ansa yana fad'in "Ameen ammh dai ka kara sani sunan Matata Hasiya ba Zabiya ba." A tare duk muka saka musu dariya ni da Hauwa'u. Kowa yaji sunan yaro sai yace Tahir ya cancanta. A gusau na yi jego na Umma da Mama na Tsaye kaina suna kula da ni. Sai dangina suka zo nan gusau karon Farko da su Adda Fati suka tako gidan su Assadiq. Wajen kwanansu hud'u sun kuma ga karamcin da mutuntatawa. Ramatu ta zo har da Inna Talatu itama Habiba ce bata zo ba tunda ta jima wajen Amma. Bani da matsalan komai ina Bangaren Assadiq Sajida na shigowa ta zauna dani mu yi ta hira kamar bamu tab'a fad'a ba. Assadiq kuma na tare da matarsa yar Rigima, Sultana dai bata samu ciki ba ta gama rigimamta ta Hakura. Ammh har yau har gobe ba wani jituwa tsakanina da ita. Ni kuma in muka had'u ni ke fara gaisheta ko da bazata amsa ba. Daga baya da taga ina tura mata Aniyarta sai ta dawo tana gaisheni in muka had'u ammh shima ba koda yaushe ba. Wannan karon na tada ma Amma Rigima sai da tazo har Gusau ta ganni ita da Matar Hamma Isuhu da Habiba da Badd'o Umma ta yi musu kyakyawan karb'a. Sai anan taga kammanina da Amma. Ta ga inda na Dauko hasken Fatata kamar ita jajir. Duk da yanayin Rayuwa da yasa Hasken Fatan Amma ya dishe ammh har yanzu da haskenta sannan Zanenta na Fulani na nan a gefe da gefen bakinta. A bangaren Umma ta sauka nan Taga su Asim sun girma da suka ganta sun manta da ita sai da suka kara ganinta sannan suka fara yarda da ita. Umma da ta kai Amma bangaran Innani tace mahaifiyata ce. Innani na saman kekenta ta rika sakama Amma albarka ta na fadin ni alheri ce ga Rayuwar magajin gida. Amma bata so ta jima ba kwana Biyu ta  sobsu yi su koma na lallab'eta ni da Assadiq ta amince zata yi sati. Anty Surayya ta zo ta gaida Amma kuma har girki ta yi ta aiko mata dashi. Ana gobe Amma za su tafi, yan'uwan Saurayin da ya ke son auran Sajida suka zo har gida har Falon Umma suka yi tijaransu. Da sunan cewa su dan'uwansu bazai auri bazawara alhalin bai bata aure ba ita kuma Sajidan suka ja mata kunnin ta rabu da d'anuwansu ruwa ba sa'an kwando ba ne. Tana bazawara sai ta makale ma Saurayi tace zata aura ko kunya bata ji ba? Umma da ta yi musu magana tace ai hakan ba Haramun ba ne. Wata cikin su ta kalleta kai Tsaye tace"Malama Rufe ma mutane baki, kinsan da haka nan da d'anki ya auro miki bazawara ki ka tada tsiyan sai ya saketa? A she wanzami baya son Jarfa ita wato ba yar ki bace tunda yanzu yarki ce kin ce ba Haramun ba ne mana." Sai Umma ta yi shuru ta koma ta na kuka Sajida ce tace su bar musu gida in Allahu ta rabu da Isma'il tunda abun ya zama haka. Har da Amma a masu ba ma Umma hakuri tunda suna wajen aka yi ni sai daga baya Sajida ta zo ta na fad'amin. Umma ta yi ta kuka ta na fadin alhakina ne ya kamata. ta tozartani da Farko gashi itama abunda ta aikata ya na dawo mata a kanta. Har Amma ta yi ta bama Hakuri akan abubuwan da ta had'a kai da ya'yanta suka yi ta min harda na korana Lokacin da na ke da cikin su Asim. Amma tace mirmishi kafin tace"Ni Hasiya ba ta tab'a gayamin kun yi mata wani abu ba, koda yaushe alherinku ta ke fad'amin na rantse da Allah ban da yanzu da kike fad'amin da bakin ki bansan da Labarin abubuwan da suka faru ba, ta Boye sirrin auranta ta zauna lafiya mu ma ta bari zukatanmu sun zauna lafiya." Umma ta yi ta mamakin halina ta kuma ta yabona a gaban Amma. Har Amma tace mata"Hasiya ta dabam ce acikin ya'yana mai Raunin zuciya ce ammh kuma mai kirki daga da yakana daga cikinta." Sajida ke ta maimata komai ta karishe da fad'in"Yanzu kina nufin har koran nan da muka yi miki ba wanda kika fad'amawa? Tab a gaisheki Hasiya." Ina mirmishi nace"To miye amfanin na yi ta gaya? Yanzu ba ga shi komai ya wuce ba, da ace na yi ta gayamusu duk wani abun da ya faru da ni sai na yafe muku su kuma su rika ganin ku da abun su kuma kasa mantawa." Sajida ta jinjina kai kafin tace"Hakane na dauki wannan dabi'ar in sha Allahu ina na samu na yi wani auren zan zauna lafiya da mijina sannan na Rike sirrinsa kuma na daina kokarin shiga Rayuwar auran wasu." Sai hawaye ni na zauna ina ta bata baki da komai taga ya faru daga Allah ne. Sai ranar da su Amma za su tafi Sultana ta zo gaisheta kuma Assadiq ya gayamata ta rika cewa saboda makaranta. Kuma Naja fa ta na wajenta Saboda Sultana Assadiq ya nemi alfarma aka basu ita har sun sakata a makaranta. Amma ko a fuska ba ta nuna ma Sultana wani abu ba. Ta dauki Ummi ta na yi mata wasa har da Goyo kunya yasa sultana ta kasa mgana. Ta ga duk rashin mutumcin da ta ke yi min uwata ta zo ta na wahala da Yarta. Shiyasa na ganta cikin masu Rakiya Abba ya ba da Mota aka kaisu har Zariya Umma ta bata atamfofi harda Hijabai Mama ta yi musu alheri Abba kuma 20k ya ba su. Naji dadi sosai bakina yaki Rufuwa abun akwai dad'i kaga an yi ma naka wani abun alherin. Zariya Amma ta wuce sai da ta kara kwana Biyu sannan ita da matar isuhu da Badd'o suka koma gida. Hankalin Amma ya kwanta na samu Rayuwar da ta ke yi min Fata Fiye da Fatan ta ma da Tsammaninta. Ni kuma wajen wata Biyu na yi a gusau sai Junior ya fara wayau sannan naje Zariya na yi ziyaran yan'uwana da kawayena. Daganan na wuce naga Amma na kwana d'aya na wuce Abuja daganan Tunda Assadiq ya rigani tafiya shi ya tafin ma da wasu kayan. Ina da sati biyu da dawowa muka je katsina gidan Tahir muka yi musu wekeend naji dadin zuwana katsina sosai. Mun zo har Daura na gaida Hajja Tana ta tambayan Innani Assadiq yace tana lafiya. Na tuna sanda Assadiq ya kai mata Tahir Lokacin da aka haifeshi ta shafa kanshi tace"Ka yi ma Attahiru takwara saura ni Magajin gida, in ka kara samun mace ka saka mata suna ba Hadiza saboda ko bayan raina ku rika ganinta kuna tunawa da mai suna na" Innani ita gani ta ke yi mutuwa zata yi ko Rasuwa aka gayamata daga Yan'uwa a shinkafi sai tace sai mun zo Allah yasa mu dace. Sai da muka dawo daga Katsina muka yi mgana da Hajiya Surayya deee na tura mata kudin ta aikomin da tsumi da kuma kazar had'in uwar gida. Ta kuma had'omin da saiwowin maganin Sanyinta Sadidan masu kyau da inganci +234 803 277 3332. Da ya ke Umma ta ba ni wasu na sha acan Sannan Anty Sakeena ma ta kawomin gumba na sha da Nono kuma na yi amfani da su. Shiyasa da Assadiq ya rab'eni yace Romon siya ya kara zak'ak'wai. Madallah da Surayya Dee madallah da Saiwowon Kazar Gudiyo da Yabi. Tunda naga na samu natsuwa Su Asim da alamu dai sun zama yan gusau nima sai hakan ya fi min dad'i. Junior ba shi da rigima in na yi masa wanka yaji Ruwan zafi shikenan sai barci. Assadiq kuma na wajen aiki sai na Tattara hankalina na maida shi kan Rubutun da na fara ina so naci karfinsa. Da karfin gwiwan mijina da taimakonsa tare da shawarwarin marubutan da na nema kan Rubutun na kamallah Rubutun bayan daukn Lokaci mai tsawo. Wanda daga baya har sai da na Sare kamar na hakura sai kuma Assadiq yace tunda na fara na karisa. Sai da na gama Tas duk na Tura musu suka Dubamu kuma suka yab'amin sosai. Auntysis ta yi min sharhi mai Tsawo sosai Anty Habiba kuma tace Rubutun da na yi bata tab'a  tunanin zan iya yin shi ba sanina da ban tab'a Rubutu ba. Surayya Dee ita ta taikamamin da Editing ta gyaramin ka'idojin Rubutu a cewarta Rubutun zai amfani al'umma zata taikamamin ya fita yadda zai zama mai kyau da amfani wajen al'umma. Assadiq ya bani shawaran na nemi cikin manyan marubutan maza ko da wata Shawaran da za su taimakamin da shi. Sai na bashi damar haka, bayan na Tambayi Lambar ALHAJI AHMAD ADO GIDAN DABINO. Na bama Assadiq ya kirasa ya yi masa bayani mutum mai barkwanci da ba ma mutane Lokacinsa. Da yardan mijina muka Tattauna da shi ya yi min jinjina sosai sannan yace zai fanshi Copy 10 in na Buga in sha Allahu. Sannan watarana in na Shigo kano zamu had'u zai taimakamin da wasu daga Cikin Littafansa da za su kara taimakamin sukara karamin kaifin kwakwalwata A lokacin dariya na yi kafin nace"Ai bazan kara wani Rubutun ba, wannan ma saboda labarin Rayuwata ne shiyasa na Rubuta." Shima Mirmishin ya yi min kafin yace"Na duba Rubutun ki, kuma na yaba miki ina da kyakyawan yakinin a nan gaba Mutane za su karu da Basirarki." Da ya ke na Tura masa shima ya Duba min tare da gyaramin inda ya kamata. A kano suka shigemin gaba na Buga Labarina mai taken TSAKA MAI WUYA.(LABARIN HASIYA) Wacce HASIYA MAMMAN KONA TA RUBUTA. A kasa kuma na saka (MATAR ASSADIQ). na kuma yi sadaukarwa ga Mahaifaina guda Biyu, Alhaji Mamman mammadi kona da Mahaifiyata Hajiya Aisha Jari Mamman. Sannan nace littafin Babban Tukwaici ne ga Mijina Babansu Asim ABUBAKAR SULAIMAN ABUBUKAR SHINKAFI(MIJIN SIYA). Na gaida yan'uwana da kawayena da suke tare dani daga Farko har karshe. Alhamdulillah ba abunda zan ce ma Allah sai godiya. Assadiq ya Dauki nauyin Buga littafin Copy 200, Tahir ya ce ya fanshi ma Hauwa'u copy goma. Adda Fati ta fanshi biyar ita da Adda Rukayya. Ramatu ma haka ita da Safiya. Abba ma da Assadiq ya gayamasa yace abu me mai kyau ya famshi Copy 30. Duka yan'uwan mijina sun fanshi Littafan nan kuma sun tayani yawo dashi domin ya samu karb'uwa cikin Sati Biyu wanda aka Buga duka ya kare, kuma ni da farko a kyauta na so na bayar da shi Assadiq yace a'a na amshi kudi ko ba da yawa ba. An sake Bugawa sannan kuma ya shiga Hannun mutane ta dalilin yan'uwan mijina da yan'uwana Tunda suna harkan jama'a. Sannan Marubuta ma sun yi min kokari sosai. Na kuma gode musu, sai bayan da na Fitar da Hardcopy da wattani uku na Fitar da Sofy copy din shi ta Kafafen Sada zumunta. Ammh Shi a kyauta na ce a yad'a shi kuma Kyauta ne na musamman ga mata da suka Fuskancin kalubale kwatankwancin irin nawa. Da yakinin cewa suma za su samu Kyakyawan Rayuwa anan gaba kamar yadda na samu. Sannan da fatan Mutane za su daina kyamarta irin mu da kaddaran kan fad'a mana sai a kiramu masu farar kafa ko wani abun da ba shi acikin Addini. Su kuma san cewa wani abun ba Aljanu ko mutum ba ne, komai daga Allah ne, sannan duk wani abu da zai faru daman ya na bukatar SANADI kamar yadda ni Hasiya na zama Sanadin Rasa dukiyar Abubakar tare da Rasa lafiya a bangaran Salisu. Sannan da kara ma zawarawa kwarin Gwiwan cewa suma mata ne, kuma masu galihu kamar sauran mata. Da kuma nuna ma duniya cewa Zawarawa ba kilakai ba ne sannan ba Yan duniya ba ne, kuma ba'a son ransu suke zama zawaran ba da yawan mu  kaddarace ta ke fad'a mana ******* *MURFI.* *BAYAN SHEKARA D'AYA.* *BBC ABUJA.* Assadiq ya rakoni ofishin BBC da ke Abuja  inda suka kirani sun gayyaceni za su yi Hira dani. Tare da Junior muka zo, sai kuma karamar jaririyar da na haifa ko arba'in ban yi ba wacce ta ci sunan Innani Hadiza muna kiranta Afra. Sanye na ke da wani less golden Mayafin jikina da takalmin kafata duka Golden ne. Ba kwalliya na yi ba tunda ban saba ba. A shekara d'ayan da na Wallafa labarina na TSAKA MAI WUYA. Ya Zaga duniya ya shiga in da ban taba Tunani ko tsammani ba. Na samu kira kirayen waya akan matan da suka fuskanci Tozarci akan Zargin Farar kafa ba adadi. Da wad'anda suke kan fuskantan haka, sannan na samu matan da sanadin zawarci ne suke fuskantar Tsamgwama daga mutane da cin mutumcin barin ma in suka samu miji saurayi ko wamda bai da shekaru zasu aura sai a rika kiransu masu kwacen maza. Matsaloli ga su nan wasu su sakani kuka wasu kuma su tunasar da ni Rayuwata ta baya. Lokacin da Ma'aikacin Bbc ya ke min tambayoyi, ya tambayeni shin da gaske ne wannan Labarin da na rubuta Labarina ne? Ina Mirmishi nace"Tabbas Labarina ne, sai dai na Boye sunayen wasu da kuma sauya  hallaya  wasu da garuruwa ammh tabas ni ce wannan Hasiyar ta cikin Labarin TSAKA MAI WUYA, wacce ta fuskanci Tozarci da kyamar al'umma saboda Canfin ina da Farar kafa, kuma ni ce na fuskancin Tashin hankalin kirana da wasu suke yi da sunan Mayya da sunaye marasa dad'i. Sannan ni ce wacce na yi aure har Biyu ta dalilina mazajen da na aura suka samu rasa lafiya da asaran dukiya, ni ce wacce duk wanda na Rab'a sai ya shiga Tsaka mai wuya sai na raba tashin hankalinn Rayuwata tare da shi." Dan jaridan ya tambayeni yadda na rika ji in kirana da sunan mayya ko mai Farar kafa? Sai naji hawaye sun kawo cikin idanuwana. Cikin rawan murya nace"Na kan ji wani irin daci acikin zuciyata sai naji kamar duk duniya ba kowa sai ni kad'ai daga baya na fara Tsanar kaina da Tunanin gwara na mutu na Huta, abun ba dadi ko kad'an shiyasa na ke so mutane su sani su kuma kara sani _BABU WANDA YA ISA YA YI MA MUTUM ABUNDA ALLAH BAI TSARA MASA CIKIN KADDARANSA BA. SAI DAI MUTUM YA ZAMA SANADI. SANNAN MU YARDA DA ALLAH MU KUMA SAN CEWA FARAR KAFA ZENCEN MUTANE NE, BA WATA MACE MAI FARAR KAFA TUNDA MU ANNABIN RAHMA KAMBUN BAKA YA SANAR DAMU._" Ya sake tambayata shin kuma bani da Aljanu? Sai da nayi dariya kafin nace "Ba ni da Aljanu ko wata matsala, kawai ni na zama SANADI ne. A Karshen Tambayoyinsa yace" Malama Hasiya daga karshe me ya baki kwarin gwiwan Rubuta Labarin ki sannan ki yad'a ma duniya? Kai tsaye ina kallon Assadiq nace"ASSADIQ. MJIN HASIYA.! Shine tsanin da na taka kuma shine gwarin gwiwar da na samu wajen Rubuta labarina na tura shi ga duniya. Kuma shine Mijin da ya aureni  duk da lokacin ina cikin Tsaka mai wuya, kuma shine ya fara nuna min cewa ba ni da farar kafa ya kuma fara sanar da ni cewa BA ABUNDA YA ISA YA SAMENI SIYA SAI ABUNDA ALLAH YA KADDAROMIN CIKIN KADDARATA.' Sannan ya aureni ina a bazawara ya zauna dani cikin Tsaka mai wuya sannan ya ji Tausayina ya tsaya min kuma ya kareni bayan ya zama garkuwata. Kafin shi mahaifiyata ta jima ta na nuna min cewa nima watarana zan samu kyakyawan Rayuwa, sai da na had'u da Assadiq na gasgasta haka." ****** Muna tafe a motar Assadiq zamu koma gidanmu. Ina gaba kusa da shi rike da Afra Junior kuma na kan jikinsa. Sai faman mirmishi ya ke yi ya na kallona, na gaji da kallona da ya ke yi yana mirmishi. Cikin yar dariya nace"Assadiq me ya faru? Hankalinsa na wajen Tuki yace"Ina Tausayama Abubakar da Salisu, domin sun tafka asaran rasa mata kamar ki Siya." Ina yar dariya nace"Allah sarki kasan da ya ganni a kasuwar kwari haka ya rika kallona ya yi mamakin ganina sosai." Da ya ke watan jiya mun je kano gidan shahida suna ta haihu. muka shiga kasuwa tare da su Anty Surayya sai gamu shagon da Abubakar ke yi yaron shago. Ji kawai na yi ya kira sunana cikin mamaki na juya nima sai na gansa na kira sunansa. Abubukar ya tsufsa duk ya yi wani iri, yace min matansa daya da yaro d'aya bai jima da aure ba. Tunda ya rasani shikenan yaji aure ya fita kansa. Lokacin muna tare da su Asim kuma ga ciki a jikina kafin na Haifi Afra ne. Har kyautar kudi ya basu har kuma muka bar shagon nan bai daina kallona ba, ina gani ya na sharan kwallah. Har ce min ya yi Hasiya ki yafemin don Allah. Ni kuma nace bai min komai ba na yafe masa duniya da Lahira. Salisu ne bamu kara had'uwa ba ammh duk sanda ya ga Ramatu sai ya ce ta gaisheni. Har muka isa gida Hiran yadda Labarina ya karb'u mu ke yi da Assadiq. Ima fad'a masa ko a yanzu Burina ya cika mata ire irena za su samu saukin Tozarci. Muna isa gida na samu kiran wata itama daga Bauchi. Tana kuma t gayamin itama ta yi aure ammh mijin ya saketa Yace tunda ya aureta ya ke ganin Bala'i mutane sun ce ita ce mai kashin Tsiya da farar kafa karshenta ya saketa. Kuma dalilin haka kowa yazo neman aurenta sai a bat'a abun ace ta na da Farar kafa wanda ya aureta ya auri bala'i da masifa. Ire iren Labarai irin nata suna da yawa, ko da yaushe cikin kuka na ke yi ina kara godema Allah. Assadiq ya zaunar da ni ya na lallashi na tare da cewa na godema Allah. Tunda ga yadda Rayuwata ta mika. Sai kuma naga gaskiya ya fad'a. Duk da dai ba ka ce ka samu komai Dari bisa dari ba ammh a kallah ka samu daidaitan Rayuwa 70% sai ka godema Allah. Kafi wani, wani ma ya fika sannan na Juya naga Ya'yana yanzu Hud'u sultana ke da Biyu itama, duk da har yanzu ba ma jituwa ammh tunda na san Halinta sai na ci mganin zama da ita. Kowa ya daina Biye mata tunda bazata sauya ba. Na duba naga hatta dangin Babanmu na Zariya ma sun daina kyamata ta tare da kirana da sunayen banza sun Fahimci ba haka ba ne. Sun  saduda sun koma ga Allah Naga duka yan'uwana mijina suna sona da kaunata sai abunda ba'a rasa ba tunda bazaka ce ka samu kowa yadda ka ke so ba. Yanzu haka Sajida ta koma gidan Mijinta sun daidaita. Sannan Su Asim suna Gusau har an saka su makaranta. Innani ma na nan da Ranta Har yanzu Lokaci bai yi ba. Sai dai a kan wannan keken yanzu ta ke Rayuwa. Na tuna Amma na can tare da ya'yan Adda, cikin kulawa da zaman lafiya sun kamata sun rike gam. Har ta aurar da Badd'o mun je mun sha biki. Sai dai mu je mu ganta mu gaisheta mu yi mata alheri. Sannan a gefe d aya Assadiq tafiye tafiye ya ke yi, tunda yanzu shima a na turasa garin da suke aiki. Sai ya yi wata baya nan ko sati uku, Sultana bata daina kishi da zargi ba, ammh dagani har Assadiq ba ma Biyemata muna kokarin nuna mata adalci. Daidai gwargwardo ba bu abunda Assadiq ya rage ni dashi, Ya bani jari kamar yadda ya yi alkawari na had'a da kudaden hannuna na kafa kasuwancin saida kayan mata, irin su less, Atamfofi, mayafai, takalma, dogayen riguna, yan kunnaye, material komai na kayan Adon mata ina Saida su, mun had'a hannun jari ni da Anty Shahida da ke kano tare da Anty Surayya mun saka a manyan kantuna kasuwan kwari, sannan gefe daya muna tafiyar da harkan kasuwancin mu ta waya, burina ya cika na zama yar kasuwar da na jima ina fata da Buri. Alhamdulillah. Idanuwana suka kawo ruwa cikin sanyin murya nace"Hakane rayuwa ta na tafiya daidai, duk da ba yadda bawa ya so ba, ammh muna godiya da irin tamu Ni'imar da ya yi mana." Rumgumeni ya yi ya na lallashima. Ya sharemin hawaye yana fadin"Ko ke fa yar Zabiyar mata ta." Na ture shi ina Dariya, zabiyar da ya kirani yasa muka Tuna da Tahir. Shima Hauwa'u ta sauka Tsakanin mu ba nisa. Sai da muka yi shirin kwanciya Assadiq na ganina da waya ya kwace ya kashe Lokaci d'aya ya na fadin"Siya yanzu fa Lokacina ne." Dariya na yi kafin nace"Ni da safiya ne kasan ni ce babbar kawar Amarya, tun ana saura sati daya zan tafi." Assadiq na hararata yace"Ko dai zaki tafi ne sai ta haihu  sai ki dawo? Kyalkyacewa na yi da Dariya sai ga Afra ta motsa. Sai ya nuna min baki alamun na yi shuru yadda ya koma ya na lallashinta ne yasa na koma Gefe ina masa Dariya, Sai da ta koma barci ya zo ta bayana ya kwanta yana fadin"Muguwa wato kina so ta hanani shagali, kinsan kuma Gobe gusau zani wajen Sultana." Ina rike hannuwansa nace"Can ma ai zaka yi shagalin ko? Kafad'a ya noke kafin yace"A'a yau romon Siya na ke so na sha, gobe sai na sha na Sultana." Mintsinan Hannunsa na yi ina Dariya shi kuma ya cijeni a kunni. Sai muka koma muna rama in rama. Kaina ya hau yana fadin"Na sauka ne ki rama? Sai na Boye kaina a saman kirjinsa ina Dariya. Ban isa na hana Assadiq shan Romonsa ba. ALHAMDULILLAH. RAyuwa ta na tafiya daidai, duk da Assadiq ba zai zama mai arziki ba ammh yana zaune damu cikin Rufin asirin da Allah ya wadace shi. Ya ci damu ya sha damu sannan ya biyamana Bukatanmu na alheri. Daman bai zama lalle ka samu abunda ka ke so duka ba in ka samu mafi Rinjaye sai ka gode masa. Kar'she. *ALHAMDULILLAH. Nan na kawo karshen Labarina mai taken TSAKA MAI WUYA, nagode ma Ubangijina domin da ikonsa na fara na kuma gama shi lafiya, ina fatan abunda na Rubuta daidai Allah ya bani Ladansa, kuskuren da ke ciki Allah ya yafe min, Dan adam tara ya ke bai cika goma ba, in ku ka ga wani kuskure ku dauke sa a matsayin ajizanci ne na Dan'adam.* *Nagode ma Masoyana da suka biya kudinsu wajen bibiyan Labarin nan tun daga farko har karshe, Nagode Ubangiji ya albarkaci kasuwanci Allah ya bar zumumci ya kuma had'amu a Aljannah Firdausi.* *Janafty*