*❣IDAN KA RAINA INDA KAKE❣* 1⃣ Na : *SAJIDA* sadaukarwa wa *ummu lalla Fatumah sisna Hawwer* Haba Aïsha, haba Aisha har yaushe zaki daina irin wannan mugun halin? Shin mai mahaifinmu ya rage mu da shi, daidai karfinsa yanai mana, du abinda muke bukata daidai gwargwadon iyawarsa yanai mana aman a kulun idan kika budi bakinki ba zaki yabi tarin alkhairan da yake yi mana na yau da kulun ba sai dai ki fadi wani wajen da ya gaza, a kulun ina fada maki ki daina kokarin hada rayuwarki da ta sabuwar kawar da kika yi.. kin ga iyayenta masu hali ne sannan samarinta sun tsaya mata...............ki........m Wace aka kiraya da Aisha wace ta yi tsai tamkar tana daukan nasihar yar uwarta ta dago fuska a hade ta watsawa yar uwar tata harara ta ja wani uban tsaki ta ce" kinga malama ki saurara min haka, shin tambayar ki nai ki yi min kari a kan tarbiyar da kike ganni bani da ita ko mai? Ni ina mamakin idan kika sakoni gaba kinai min fada tamkar ke ce yayar tawa ni kuwa kanwarki,,, idan ke ita rayuwar nan ta yi maki sai ki je ki karata da talauci aman ni na fada maki idan baba ya nacewa FASKARE ni ba zan iya ba, ga ayuka nan barkatai a duniya aman shi ya nace sai dai faskare da shi ne zai ciyar da mu? To zan fada maki ko ta tsiya sai na shiga banban gida na hau babar mota domin Allah ya bamu halin auren nairar tunda ya kayatar da halitar mu....... Ta gama tana mai juya dara daran idannuwanta ta zarce wajen dan karamin madubinsu ta zauna ta shiga fence fuskarta Ta jima zaune tamkar ruwa ya cinyeta tana mai takaicin halayar yayarta, a hankali ta mike ta karaso kusa da ita ta dora hannunta na dama saman kafadar yayar tata ta marairaice murya ta sada kanta alamar zata bada hakuri ta ce" ki yi hakuri Autyna, ban fadi haka dan na bata maki rai ba idan na ga irin haka na faruwa ne sai hankalina ya tashi domin bana so ki fada *tarkon samarin zamani ne* inai maki son da ba zan juri ganinki a wani hali ba plz auntyna ki yi hakuri kar ki yi fushi da ni A hankali Aisha ta juyo ta kamo hannun kanwarta wato *RAUDA* wace take yiwa kiranye da LALLA ta ce" *LALLANA* ki gane ni du abinda ya shafi talauci batan raina yake, ki duba fa ki ganni kulun Abanmu jalabiyarsa kwaya daya ya fice da ita da gatari ya tafi yawon anguwa anguwa kofa kofa yana neman itacen da za.a bashi ya faskara, bayan ya gama a hada shi da naira ashirin naira talatin baban samunsa naira dari watarana sai ya wuni bai samo komai ba ya dawo haka zasu yi ta samun matsala da mama sannan da wannan samun ne yake ciyar da mu ya siya mana atampa roba ya yi mana dinkin naira dari bibiyu, sai fa sallah ta zo bamu da kayan sallah dududu har muka yi yarinta muka gama hijabanmu hudu a duniya muna arawa juna muna canzawa...... makaranta litafinmu kwaya daya da shi kike rubutu nima da shi nake yi.... haba ko yaya na ga haske ai zan nufe shi shi ya sa nake fada maki yanzu mun taso mun kai mizanin yin samari muna jami.a dole mu so daukan wanka ko dan gudin raini , sannan samarin nan harin mu suke ina mai baki shawarar ki kula su tun suna kula ki ba sai su yarda ke ba ki dawo kina zubar da kwalah kina haukan neman su Ajiyar zuciya Rauda ta sauke, kwata kwata magangannun yayarta banda caza mata kai ba abinda suke... a kulun adu.arta shine Allah ya katsewa yar uwarta irin wannan dogon buri na mahaifiyarsu tun kafin ya zame mata matsala, ita bata ga abin damuwa a rayuwarsu ba mahaifinsu yana nema tun karfinsa da shi yayi ta fafutuka wajen gannin sun yi karatu sun samu ilimin adini da na boko, da yake mutun ne mai tsayuwar dare mai fawalawa Allah lamuransa sai ya kasance duda makarantar gomnati suke yi sannan a jarabawa basu da mai kama masu sai Allah Ya tsaya masu suke tafe cikin nasara har Aisha ta samu shiga University sannan Rauda...... manema aurensu kuwa ta ko.ina fitowa suke sai dai idan har sunanka bai zarce ba Aisha Bata sauraronka ita kuwa Rauda tana saurare sai dai mahaifiyarta ta shiga ta fita ta kori mutun sannan ta.... Tunanin mai kike ne Lallana? Muryar Aisha ya kashewa Raudat tunanin da ta fada ta zabura ta kakaro murmushi ta ce" ba komai Auntyna , Allah ya shige mana gaba Aisha ta amsa da amin sannan ta juya ta ci gaba da gyara fuskarta dan zuwa makaranta Haka suka fito Aisha ta gyara fuskarta tamkar zata je wajen biki Raudat kuwa banda kwali da ta dan furta a idannuwanta ko hoda bata shafa ba Mahaifinsu ne zaune yana wanke hannunsa da gatarinsa gefe ya saka jalabiyarsa wace dan tsufa har yamutsewa take sai hularsa irin zigegen alhazan nan wace a kadan ta shekara hudu da aka yi masa kyautarta Amsa gaisuwar yayan nasa yake cikin sakin fuska da basu mahinmanci sannan ya shiga laluben aljihunsa ya jawo naira dari da ashirin ya mikowa Aisha wace ita ce baba ya ce" Aisha ga wannan ba yawa sai ku sha ruwa a hanya Aisha ta bi hannun mahaifin nasu da kalo naira darin ta yakune du a cicire hakama ashirin din ta sama ta kakaro murmushin yake ta ce" baba ai ka barshi kawai Tana gama fada ta mike ta fice inda suka rakata da kalo jikinsu ya mutu murus A hankali ya juyo da dubansa wajen Raudat , Saurin basar da abinda Aisha ta yi ta yi ta kakaro murmushinta mai kyau da tsari ta mika hannu biyu ta ce" Lah Abanmu ni dai ina so, bani naira ashirin din sai na kara da sauran canjin da ka bamu jiya bamu kashe su duka ba shi ya sa aunty ta ce bama so, tana son cewa ai da saura ne Ta karasa maganar tana karbar ashirin din da iya kokarinta dan gannin ta mantar da shi dabi.ar yayar tata Murmushi yayi ya sakar mata ta mike ta kama hanyar fita Har ta daga kasarin da ya kare kofar mahaifinta ya ce" *Raudat*... A hankali ta juyo tare da amsa kiransa Cikin murya mai cike da nutsuwa ya ce" Allah ya datar da ku da dukan alkhairin rayuwa, ya daukaka ku, ya sanya farin ciki a cikin rayuwar ku, ya baku mazaje na kirki masu tsoron Allah da bin umarninsa , A hankali take amsawa da amin a dukan adu.ar mahaifinta har inda yake cewa" Allah ya shiryar da yar uwarki tun kafin dama ta kubuce mata, ya sa ta daina hangen na wasu ya kasance ta daina *raina inda take kar taje ta yi biyu babu domin mafi yawancin irin haka inda zasu ya raina su* Saurin dago da kanta ta yi bata ce komai ba sai lumshe idannuwanta da ta yi ta mike ta kara gyara hijabinta ta juya tana sauri kar Aisha ta yi tafiyarta Wani irin haushi da bacin rai ne ya turneke mata zuciya hango yar uwarta da ta yi tana kokarin shiga motar sabuwar kawar da ta yi mai suna Aminah Dan tsayawa Aisha ta yi tana kalon Yannayin Raudat, dan haka ta hade fuska danma kar ta kawo mata wargi gaban Amina Tana karasowa ta ce" mu je ko? Kin ga Allah ya kawo freind ba sai mun sha wahalar tafiya kafin mu hau bos ta sauke mu a bakin titi mu kuma yin wata tafiyar kafin mu karasa jami.a Ta karashe tana dage gira dudan ta shawo kan Rauda duda ta san abu ne mai wuya ta yarda ta shiga dan ba shiga take yi ba Rauda ta dan kakaro murmushi ta ce" ai kin san ina son tafiyar kafar nan ko dan na dan ringa mike kafana aunty ku je kawai sai na karaso Tun kafin ta gama maganar Aisha ta daga kafadu irin ke kika jiyo ta bude gaban motar ta shige Amina ta ja da mugun gudu suka bar wajen Ajiyar zuciya Rauda ta sauke ta daga kafa ta nufi bakin titi dan shiga bos ta kaita makaranta Lecture din awa hudu ne da ita a yau, haka ta yi karatun nan ba tare da ta saka komai a cikinta ba dan tana son kudin su isheta komawa gida Karfe 2 na rana suka fito ta nufi bangaren su Aisha dan gannin ko basu sauka ba ta yi jiranta sai dai mai tana karasowa ta tardo Amina kawar Aisha ta kwashi wasu yan mata a motar nata tana baiwa Aisha hakuri cewar zata sauke su ita ta yi hakuri gobe sai ta dauke ta, cikin raini da isa take fada mata hakan Aisha ta yi sororo jikinta ya mutu ta kasa koda daga kafa ta bi motar da kalo har suka kai bakin gate din agriculture suka fice har ta daina hango su aman ta kasa daga kafarta A hankaki Rauda ta ce" aunty, mu tafi plz ai har sun bacewa ganinki kina tsaye, Da sauri ta juyo tana kalon rauda , maganar rauda ya fado mata inda take cewa" Aunty a duniya idan kina son ganin wulakanci ki kwalafa rai da *abin mutun* komai kusancinki da shi ya kasance kina nesa da abinda yake malakinsa ne hakan zai saka tarayarku ta jima sannan mutuncinki ya dauwama a rike a wajensa Idannuwanta ta lumshe wa.inda suka yi jajajir ta ce" WALAHI WALAHI WALAHI SAI NA HAU MOTAR DA TA FI TA AMINA SAI MURZA NAIRAR DA KO UBANTA BAI MURZA BA.......... Baki bude Rauda ta bi yayarta da kalo, inda gabanta ya tsananta faduwa har ta furta tambayar " *AUNTY ta ina? Ta yaya? Ta wace hanya kike irin wannan tunanin?* Aisha ta ja tsaki ta ce............. Shan koko bukatar rai😍❣😍 *❣IDAN KA RAINA INDA KAKE❣* 2⃣ NA: *SAJIDA* Allahuma ajurni minna nar......👏🏻 Aisha cikin kakausar murya ta ce" ki sani Raudat, ko ta hanyar Allah ko ta tsiya sai na yi kudi sai na kamo kawayena sai na shiga motoci , sai na rike babar waya sai na kwatarwa kaina inci na arziki Ran Rauda ya baci iya baci hakan ya saka ta shiga hawaye wanda mafi akasarin lokuta hakan zaka ga yana faruwa idan ranta ya baci wajen mutumin da ba yanda zata yi da shi sai kawai hawaye su balewa idannuwanta Juyawa ta yi kawai ta bar yayarta a nan dan ta lura Aisha fa ta yi nisa bata jin kira, burinta na ta zama mai kudi ko ta auri mai kudi ya girmami tsoron Allahnta (wa.iyazubillah) A wannan rana kowace ta dawo gida ne ranta a bace ba mai yiwa yar uwarta magana Suna zama mahaifuyarsu ta shigo, tun fitar karfe shiga da ta yi da sunnan ta tafi gidan biki sai wannan lokacin ta dawo da leda a hannunta Fuskokin yayan nata ta bi da kalo ta dasa ayar tambayar abinda ya dauke annurin fuskokin su Ansa gaisuwar Rauda take hankalinta na kan Aisha ta katse amsa gaisuwar ta ce" *Jarina* wani abin ya faru ne? Nake gannin fuskokin naku du a hade ko abin da ta saban ne ta yi maki???? Ta karashe tana zabgawa Raudat harara Aisha ta kara hade rai ta shiga kwararowa mamansu abinda ya faru Ran mamansu Raudat ya mugun baci da wannan cin mutunci da kawar yarta ta yi mata, cike da bacin rai ta ce" mai ta fi ki? Kyau fari gashi sura ko mai? Abinda ta fiki uba mai "Takaici" ita mahaifinta ya gane cewar faskere banda kashe zuciya ba abinda zai hadasa masa, ya fahimci cewar mutunci kankaro shi ake sannan kudi su ne jin dadin gidan duniya idan babu su sunanka wulakantace kaskantace marar galihu Tunda ra fara fadan nan kan Rauda yake sade a kasa tana sharar hawaye a kasan zuciyarta tana fadin ikon Allah wannan shine wani da aikata laifin wani da shan duka Dan haka nake fada maku ku mu tashi mu nemawa kanmu yanci... Wannan rayuwar talaucin haka na sha ta tun da jan sahunna wai ni soyaya... a soyayar nan banda tsufa da karewa ba abinda ta kara min , ku fa sani ba soyayar nan ake ci ba idan tafiya ta yi tafiya baka da abinda zaka zama sai abin "tausayi" Aisha ta bude idannuwanta ta ce" mama, ki daina bata yawun bakin ki domin ni nan da kike ganni talauci shakar kanshinsa sai dai idan na shigo gidan nan kafin mu kenkyara namu mu koma....... abinda Amina ta yi min ban ga laifinta ba domin wa.inda ta dauka yayan masu fa shi ne A gaskiya mama ke kika cuci rayuwar mu da kika auri baba..... ni nakan rasa amsar tambayar mai kika gani baba dai ba wani kyau ba gaba daya ke muka biyo bafilatanar usil aman kika auri mutun irin baba Ta karashe maganarta fuskarta na nuna tsantsar bacin ranta a lamarin Mahaifiyarsu mai suna nana Mariama ta ce" uhum ke dai a bar naganar kawai , kun ga fa fogayen riguna na gani na sayo maku sai dai kwaya uku ne maimakun hudu dan haka ke Rauda ki yi hakuri da dayar Gaba sai na kara maki Rauda kam bata cewa komai tana bin su da kalo nan Aisha ta shiga dadaga kayan tana ta murna domin kaya ne masu kyau duda ba masu kudi da yawa bane Cikin mutuwar jiki Raudat ta mike ta shige dakinsu ita da Aisha Zama ta yi gefen katifar su ta kurawa madubi ido tana kallon fuskarta a ciki A hankali ta lalubo hoton mahaifiyarsu inda take ganiyar kuruciya ta zubawa hoton ido A jikin hoton bata fi shekara ashirin ba komai na cikakiyar mace akoyshi a jikin ta Ajiyar zuciya ta sauke a fili ta ce" shin ikirari takama da su mama suke yi da kyau da yarinta da kalar fata bata lura aya ta kasance a kan kanta ba? Ita da ta yi gadon kyan gaba da baya wajen mahaifiyarta da mahaifinta bata ga yanda yanzu fatarta ta dawo ba? Duda tana fadin cewar wahala ta dawo da fatarta haka aman ai daman kuruciya kyau ba madawama bane, ita fa a ganinta ai gwara ka yi anfani da kyan naka wajen aikata alkhairi da shi ka kilace shi ka rufe shi ya anfaneka sai mijin da ka aura ba? Da ka biyewa rudin dun....... .......... Tunaninta ya katse daidai lokacin da Aisha ta jefo mata jar riga cikin rigunan wato ra zabi kala biyu ta bata guda sannan ta ce" ki tashi mu je mu dora tukunya mai nemowar ta kawo mana yau nama zamu ci,.... kai da ba dan Mama ba da mun yi anagon nama da sai muna tafe muna kalo a wajen masu siyarwa Mikewa Rauda ta yi ta cire hijabinta ta shanya shi saman yar igiyar da suka kula suke shanya kananun kayansu a dakin nasu ta daura dan kwali ta fito Itatuwan da mahaifinsu ya sara ya kilace masu fan dora tukunya ta fauko kwara hudu ta ajiye gefe ta share cikin murhun da bakin murhun ra hada tokar ta kai cikin shara bakin kofar gidansu ta dawo ta tsintsinto ledoji busasu ta karaso bakin murhun ta saka itatuwan ta hasa wutar Juyawa ta yi tana kara wanke tukunyar sanan ta dora saman murhun ta dawo ta zauna tana wanke naman nan tana zubawa cikin tukunyar bayan ta gama ta kawo kayan yaji atarugu da gujiyar miya dakakiya ta zuzuba ta rufe ta juya ta shiga yanka albasa kananuwa domin so take ta yi ta gama fan du infa mahaifinta yake ya kusa karasowa gida Nana mariama ce ta fito da tarin tafarnuwa a hannunta tana fada ta ce" daman na san ba zaki zuba ba dan ubanki yace baya ci sai kika manta cewar ni na nemo na kawo shi abinda ya iya kawowa masara da gero ne, malama karbi ki zuba min a ciki tun kafin ranki ya baci Raudat ta dago da kanta tana fan share irin hawayen nan na zafin albasa ta ce" haba mamanmu, naga ai mu idan da akoy ko babu ma muna iya ci ko? Mai zai hana idan na gama na fitarwa da baba nasa sai a zuba a namu mamanmu? Kinga ba kyau ka ci tafarnuwa ka je masalaci domin ita warinta yana fa naci ne, yakan zaunawa a jikin mutun na tsawon lokaci koda kuwa ya wanke bakinsa , ki yi hakuri idan na fitar masa da nasa sai mu saka Nana Mariama cikin bacin rai ta dauke Rauda da mari, daman ita akoy saukin hannu ga zafin zuciya ta ce" ki shiga a taitayinki Raudat, ke banda shirme irin naki mutumin da datin jikinsa ma ya ishe shi shine zai fito mana da karyar wai shi baya cin tafarnuwa? Yaushe ma ? Sannan ki bari idan ya shigo gidan nan da leda dauke da nama sai ku yi mana iya yi Tana gama fada ta bude tukunyar ta afka tafarnuwar sannan ta juya ta yi tafiyarta aka bar Raudat da takaici Zaune yake yana irga kudin da yayi a yau, cike da farin ciki domin wata mata ya samu irib masu kasa itacen nan ce sannan bata da bakin ciki ta bashi faskaren mai yawa wanda sai da ya kasa shi uku ta biya shi wajen dubu guda da dari uku Bayan ya gama irgawa ya shiga tunanin mai zai yiwa yayansa da matarsa dan ya faranta ransu???wani mai siyar da takalma ne irin na robar nan na mata bakake da chocolate ya zo ficewa hakan ya saka Malan Ahmad mikewa fa dan hanzarinsa ya tsayar da mutumin ya dauki taki uku bakake biyu da chokolate guda suka yi cikini Da kyar ya bara masa su a dari takwas ya biya cike da farin ciki ya dauki hanya da naira dari biyar din da ta yi saura yana ayanawa a ransa cewar gobe idan zasu tafi makaranta naira dari bibiyu zai basu ya tabata Aisha zata yi murna da hakan (😭) Da salama sannan da karfinsa ya shigo gidansa , inda ya tarar da iyalinsa kyawawa zaune saman tabarmar ledar dakin matarsa suna hira sannan ga abinci suna ci cikin annashuwa Ba yabo ba falasa mai dakinsa ta amsa gaisuwarsa inda Raudat t mike d sauri ta karbi ledar hannunsa da gatarinsa tana ta jera masa sannu da zuwa ta kai gatarin ma.adaninsa sannan ta nufi dakinsu da ledar Cikin fara.a ya ce" Raudana aa wannan naku ne mikawa mamanku Cike da murna ta mikawa mahaifiyar su ledar wace ta dago a yatsine ta karba tun kafin ta bude ta ce" ba girin girin ba dai ta yi mai Fitar da takalman take a yatsine sanna ta dago tana dubansa wanda yayi kasakai yana jiran gannin fara.a a fuskarta sai dai kashhhhhhh abinda fuskarta ya bayanar masa sai yayi dan daman ma bai shigo gidan a wannan lokaci ba Ba tare da ra bayana farin cikinta ba ta mike ta zubar da su a nan ta kare yi masa kalo ta shige dakinta A hankali aisha ma ta mike ta yi kamar bata ga abinda ake yi ba ta kwashe kwanon namanta ta shige dakinsu A tare suka raka su da ido, Raudat ra yi gagawar mikewa ta kwashe takalman, tamkar wata yarinya karama ta shiga murna harda dan tsalanta ta matsa wajen mahaifinta ta kamo hannunsa ta ce" Abanmu, kamar ka sani kuwa takalmanmu sun tsufa, kai Abanmu Allah ya kara budi ya saka maka fa gidan Aljannah ya kara maka wadatar zuciya da arziki mai anfani Bai amsata ba, sai wani ciwo da yake ji yana kara yin sama a zuciyarsa A hankali ya mika hannunsa wajen fuskarta da ta jajir ga sawun yatsutsai wanda du idan an taba lafiyar jikinta baya buya yakan shaida kansa ne koda kuwa an kwana Dan shafawa yayi ya dago jajayen idannuwansa ya zuba su a kan fuskar yarsa, wace shi yayai imanin da bata tare da shi da tuni zuciyarsa ta buga a irin halayar matarsa da yarsa ta fari, cikin yannayin damuwa ya ce" RAUDANA kin tsokani magana bayan bana nan ko??????? Rauda ta ce..... ....... ...... ....... Tafiya sannu kwana nesa❣ *❣IDAN KA RAINA INDA KAKE❣* 3⃣ Na: *Sajida* Raudat cikin mutuwar jiki da abubuwan dake faruwa a gidansu da mugun tausayin mahaifinsu ta sada kanta ta ce" babanmu ba komai Dan murmushi ya kakaro ya dauko canjin aljihun nasa ya rage naira dari kawai ya mika mata ya ce" Raudana yau alhamdulilah an yi samu sosai, kin ga canjin na rago maku ki baiwa yar uwarki Tamkar ya malaka mata duniya haka ta yi ta godiya tana kwararowa mahaifinta adu.a wace tanai masa a fili shi kuwa yanai mata a zuciyarsa a haka ya juya ya fice dan gabatar da sallah a masalaci Washe gari ya kama ranar laraba, tun da safe yar karamar wayarsu wace Aisha ta zamneta take ringin , kira na uku ne Amina ke kiran wayar aman Aisha taki dagawa dan cike take da ita Ran Rauda fari kal tana adu.ar Allah ya sa tarayar tasu ta kawo karshe domin sam ba alkhairi a wannan taraya tasu A hankali ta warware rigar wajen mahaifiyar tasu domin yayarta ta dage sai sun saka su yau ta dora saman kananun kayan da ta saka wankaku tas Jiyowa ta yi ta saki baki cike da mamakin yayar tata, somin ta daga wayar ta bude kararta tana yatsina tana ci gaba da fente fuskarta ta amsa da ina jinki Daga dayan bangaren Amina ta ce" sowi kawata , na san jiya ban kyauta ba aman ki gane motarta ta samu matsala shi yasa kuma kinga su basu saba shiga motar haya ba shi yasa nace bara kawai na kai su aman yanzu ki yi ki fito zan zo na dauke ki kin san fa yau bamu da lecture da yawa Aisha ta yi gagawar katseta da fadin sai kin zo, dan kar ta idasa maganarta Rauda ta kifta idanuwanta cike da mamakin yayar tata, aman kuwa lale wani rashin zuciyar ma mai ake da shi Yaya dai??? Aisha ta jefowa Rauda tambayar tana mai bin yanda rigar rauda ta mugun yi mata kyau harma ta fara kokonta a kan zabanta da ta yi na rigunan Rauda ta kawar da kanta tana kokarin warware gugar hijabinta da ta yi fari kal mai hannu sannan ga tsayi har kasa ta ce" gani na yi jiya jiyan nan kika gama rantsuwar kin daina shiga motarta aman yanzu ta yi kiranki bama dan ta baki hakuri ba sai kara caba maki magana da ta yi aman du da haka kika amsata da sai ta zo? Rauda kina da motar da zaki kaimu ne? Ba gaskiya ta fada ba cewar nice na saba da yawo a bos aman su mai suke da bos motar talakawa? Shin idan na yi fushi ta ina zan samu hanyar zama watar? To kinga ki saurara min binta zan, sannan idan kina zuwa gaskiya ba zamu daukeki da wannan hijabin haka sai kace wace zaki tafi masalaci mtsssssss " Aisha ta karasa maganarta da jan wani uban tsaki Rauda ta sauke ajiyar zuciya sannan ta bi hijabin jikinta da kalo, ta kuma dagowa ta kali yayar tata sai kawai ta zura hijabinta ta lakaci mansu mai maski ta dan gogawa lebenta ta juya ta shiga harhada takardunta Tana kalo yayarta ta yaye kanta da dan kwalin rigar wanda hakan ya baiwa dogon gashin kanta damar fitowa a bayanta sosai sannan daga gaba ma yayi konce gaban goshinta ana ganinsa sosai Takalminta plat ta dauko ta saka sannan ta dan goga turarensu da ya dauko hanyar karewa ta fice ba tare da ta kuma fustawa Rauda kalma daya ba Itama cikin nutsuwa ta gama ta fito ta nufi wajen mamansu ta ce " umma zan tafi Dago kanta ta yi ra zuba mata ido, kamar mai nazarin wani abin sai can ta ce" oh to ni dai Rauda ko dai wani kasurgumin ustaz zaki aura? Na cire kudina na sayo maku rigunan aman dan wulakanci shine zaki hadata da wannan uban hijabin da ubanku ya saya maku? Shiyasa ashe Aisha tayi tafiyarta ta barki kina fama da hijab Ita dai kanta a kasa bata furta komai ba har mahaifiyarta ta gama fadanta ta ce" na tafi umma Ajiyar zuciya Nana Mariama ra sauke ta ce" a dawo lafiya Allah ya bada sa.ar tafiya Ta yi murmushi ta juya da kudaden da mahaifinsu ya basu, bata tsaya nemansa ba dan ta san idan ransa a bace sabkon fita yake Tafe take tana sauri dan isa bakin titi wani mai adaidaita ya zo ficewa ta tsayar da shi dan ta yi lati sosai , sai dai mai adaidaitan ya ki ya dauketa koda a naira dari da hansin ne , haka tana kalonsa ya tayar yayi gaba abinsa Tana isowa bakin titi ta tsayar da bos yafi a kirga sai dai du a cike basa tsayawa da kyar ta samu guda wace ita dinma ta kudan cika domin an tsatsaga mutanen sosai sannan harda maza a ciki Yaron motar ne ya fito ta kare mar kalo, garjejen kato ne sai wari dati yake , a hankali ta ce" dan Allah malan ku dan matsa na shige ciki Kowa yana muzurai suka dan ja kafafuwansu ta samu ta shige can ciki jikin window ta makale tana neman sheda Haka suka ja motar nan suna tafe suna tsayana suna sauke wasu suna daukan wasu Daidai danja motar ta tsaya suna jira a sake su Kan Rauda a kasa tana dan jan nunfashi tana share gumi da dan kyanlenta mai tsafta tana dan hura hijabin nata Kamar ance ta dago da kanta sai idannuwanta suka sarke da wani mutun a zaune a bayan wata wuleliyar mita baka sai dai gilashin motar ana gannin na ciki kamar yanda yake gannin na waje, Abinda ya bata mamaki sai ta ga tamkar gala mata harara yake, kwarjininsa ya saka mata faduwar gaba hakan ya sa ta sada kanta aman mai sai zuciyarta ta dameta da son sannin shin hararan nata ne yake da gaske ko kuwa? Kuma dago da kanta ta yi ta dan sato kalonsa aman mai tabas harara ne yake gala mata irin mai cike da haushin nan Cike da mamaki ta bi motar da yake ciki da kalo daidai lokacin da danja ta saki motocin suka fice shat shat tamkar iska ke tafe da su Bata san tana sauke ajiyar zuciya ba har sai da na kusa da ita ya ce " malama sannu kin matse ko?? Kawar da kanta ta yi domin wani irin warin baki ne ya daki hancinta daidai motar ta tsaya wajen jami.a Da sauri ta sauka ta biya kudin ta yi gagawar sayan piyawata ta cira ta kwararawa fuskarta ta shiga sauke ajiyar zuciya tamkar ta yi tsere .......... A wannan rana sai ta rantse bata ga anfanin zuwanta makaranta ba domin da ta shiga aji bata samu gabagaba ba sai can baya dan an jima da fara lecture, inda ta samu kuwa daman wajen zaman yan bata aji ne banda labarai ba abinda suke Suna fitowa ta zauna tana duba litafenta Wata sansayar murya ce ta yi mata salama cewar"asalamu alaiki ya ke ma.abociyar kyau Bata dago da kanta ba aman bata ci gaba fa karanta takardar ba ta yi tsam ta shiga tunani, Wannan mutun wanene? Du inda na yi yana biye da ni, shi ba wani mai shekaru ba ko daga kalon fuskarsa aman du inda ya ganni ya kama kure min kalo sannan kokarinsa mu kasance iya mu ya samu damar yi min magana Du wannan magangannun cikin zuciyarta take yi jin shiru ya saka ta dan dago da kanta tamkar mai tsoron ya kamata Murmushi ya sakar mata yana mai yi mata irin kallon kurullahn nan Hade fuskarta ta yi, ta sada kanta kasa Gannin haka ya ga a yau fa wannan itace damarsa wace idan yayi wasa da ita may be ba wata Muryarsa ya kara sasautawa tamkar munafuki ya ce" na tabata zaki cewa zuciyarki wannan mai nacin haka fa? Ki yi hakuri ko na hakura zuciyara sai ta shiga fada tana tsale tana fadin dan me ai itama mai inci ce dan haka ke ta zaba Wani irin gingirigin take jin zancensa, ba wai dan bata saba ji ba aa sai dan wannan da salon yan gayu a ciki Dago da kanta ta yi a karo na biyu, yana da kalar nutsuwa, yana da matsakaicin tsayi sannan kakaura ne bashi da rama ko kadan, irin mazan nan ne masu kiba harda dan tumbinsa na fura(😂) Katse mata tunani yayi da fadin" sunana Abdurahaman, ni ba kowa bane sai mai nema tun karfinsa, ina da shago a rijiyar lemu ina siyar da kayan yan mata da na mak up, daifai gworgwado ina da rufin asiri sannan ina karatu a wannan jami.a inda nake karantar kasuwanci domin wannan rayuwa komai sai da ilimi, na taba aure matata ta rasu tun kafin ta tare, hajia Rauda na jima ina bibiyarki a gaskiya nutsuwarki ta fi kwadaita min son kula alaka ta alkhairi da ke, na sani ke din kalar manya ce aman na zo da kokon barata zan hau takara idan rabona ce kinga ai sai hamdallah , ya karashe yana mai sakin dan murmushi Tausayin kanta ne ya dirar mata lokacin da ya kawo aya ta tuna maganar mahaifinta inda yake cewa *Raudana kinga rayuwa ki yi fatan samun miji na gari, kar ki yarda rayuwar wani ta rude ki ko ki sakawa kanki dogon mafarki wanda ba zai fishe ki ba, ita duniya komai Allah ne mai yi, kina iya nacewa mai kudi ki zo ki aureshi ya talauce, dan haka ki barwa Allah zabi du wanda ya fito maki idan mai mutunci ne ki amince a yi maki auren ki domin ni dai a yanzu banban burina shine na aurar da ku kafin kasa ta rufe idannuwana....* , babar damuwarta mahaifiyarta domin ita fa a wai take ji wai zata so da namiji, wani irin so kuma? Kawai sai ta kali garjejen kato ta ce masa tana sonsa? Ita wani abu ne zai kaita ga aikata haka? Bata tunanin kyau isa ko arziki zasu yi tasirin karkata mata tunani haka aman ance idan aka zauna da mutun anfi shakuwa da shi, ta sani bata taba kawo koda mai keke ne gidansu ba hakan ya saka mamansu ke koran dukan manema aurenta tun tasowarta shekara goma sha biyu har zuwa yanzu da take cikin ta ashirin da daya , wannan bawan Allah harda mashin dinsa wanda take ganinsa yawancin lokuta a sama, tabas zata saurareshi koda kuwa a kansa ma bata ji soyayar ba idan Allah ya sa shine mijinta shikenan ta yi aurenta Abanta ya samu konciyar hankali A hankali ta ce" ka yi hakuri, ka bani lokaci zan je na yi shawara Murmushi ya saki, ya ce " ki taimaka wajen shawarar nan ki yita da mai kaunana Dan murmushi ta saki domin ya bata dariya wai da mai kaunarsa, ta sada kanta kasa ta mike ta tatara kayanta inda ya bita yana magiyar ta zo ya kaita gida aman fir ta kiya karshe ma sai ta tari adaidaita ta mika masa duka canjinta ya dauke ta suka dauki hanyar gida Mita na tsayawa ya bude ya sauko ya shiga taku cikin hanzari ya shige part dinsa ba tare da ya waiwayi kowa ba Yana shiga ya rufe dakinsa ya dauko remote ya danna ac ya kara masa gudu dakin ya garwaye da kanshi da kuma sanyi Botiran maroon din jalabiyarsa ya bale daga gaba, ya konce dan nadin da yayiwa kansa tamkar balarabe ya fada gadonsa da baya yana fadin" bismillahi rahamanin rahim Daga bakin kofa ake buga masa kofarsa ya bata rai ya dago hannunsa na hagu yana dubawa ya ga karfe 12 ne yayi A hankali ya furta" ai ba zuwa kasar ba , auta ta dami mutun, yama aka yi ta sauko da wuri haka????? = domin kaf gidan nan ba wanda ya isa ya ratso kofofin nan ya zo har bangarensa sai ita ! Dan kuwa baka ga fuska bama bale har ka rabe shi, wai danma ya zurfafa a adinni domin har sunna sukai masa da ustaz.... Mikewa yayi ya mayar da botiransa ya bude kofar sannan ya saka hannunsa ya kare danma karta shige masa daki dan kuwa ransa a bace yake Fuskarsa ta karewa kallo, gannin ransa a bace ya saka ta daina fada masa abinda tayi niya, ta ce" big broth what happen???? Idannuwansa da suka canza kala ya lumshe a hankali ya ce" ina son komawa saudiya Ido ta zaro, a ranta ta furta komawa fa tap, ai ka zo kennan dan kuwa naji Aba na fadin saudiyar nan ta isa haka kuma ka zauna a kasarka Murmushi ta yi ta ce" haba yayan *Hafsa* , mai yayi zafi harda zai kone? Mu muna son ka zauna da mu plz yayana, Ajiyar zuciya ya sauke ya rufe dakin ba tare da ya bata gamsashiyar amsa ba Cike da sanyin jiki ta koma, ita fa abinda ta yi niya sai ta yi domin so take ta yi masa birthday na surprise ta gayato kawayenta harda kawarta *AMINA* dake mugun son koda magana ne yayanta yayi mata Yana rufe dakin ya ja wani uban tsaki, a fili ya furta" ba zan iya zaman garin nan ba, kana tafe ne ranka na baci , a cikin tafiyar hanya ma zai ka danne zuciyarka karta buga da abin haushi ina da ka zauna zaman dindindin, yanzu in ba rainin hankali ba macece fa ta shige can ciki maza sun saka ta a tsakiya haka tana shakar shedar su suna shakar nata koda maharamanta ne shi sam bai ga dacewar hakan ba ( wayo Rauda a bos🤣 ) Haka yayi ta fada shi kadai har lokacin sallah yayi ya mike ya shige bayin dakin nasa .......... (Wannan kennan ) *❣IDAN KA RAINA INDA KAKE❣* 4⃣ Na: *SAJIDA* Bayan kwana biyu Zuru Aisha ke zaune a tsakar gidansu tana kallon waje guda , yannayinta ya nuna tana cikin tsantsar damuwa Mamanta ne ke zaune a bakin murhu tana faman kada miyarta ta kuka da ta sha kayan hadi ba laifi Dayan gefen kuwa Rauda ce zaune ta dukar da kanta kan litafin adinni tana ta tilawa Mama,..... " Cewar Aisha cikin sanyin murya Dago da kanta ta yi ta amsa tana kalon yar tata Aisha ta sauke ajiyar zuciya ta ce" Mama, kawar Amina ce ta gayaci amina gidansu, ita kuwa ta gayace ni ana wani sabga a gidan, mama kayan da kika kawo mana gaba daya na saka du sun ganni da su, sannan gidan gida ne na manya baki ga yanda Amina ke rawar kai tana murnar zata je gidan ba, shine abin ke damuna kuma abin nan ya kama gobe ne da safe .... ban san ya zan ba Shiru Nana Mariama ta yi ta afka tunanin ya zata yi ta taimaki yarta? Ba tare da ta tambayi wace irin sagba bace, sannan ba ruwanta da sannin ina ne, abinda yarta ta fada cewar suturar da ta kawo masu du ta saka tana jin kunyar a kuma ganninta da ita bai dameta ba a matsayinta na mai neman cin yau .... sai ta fahimci hakan a matsayin kankarowa kai girma, sannan abu guda ta san idan dai ta yiwa Aisha sai ta yiwa Rauda domin du inda zata je dole sai rauda ta raka ta wannan kam ta kasa hana wannan dokar ta malan du nacinta Cikin nutsuwa ta ce" karki damu Shine kawai abinda Nana mariama ta fadawa Aisha wanda ya saka ta washe ta mike ta shiga shiryawa wannan tafiya ta gobe ta hanyar kyalkyale kyalkyalen kafafuwanta da shafa masu man bulanga dan su kara taushi su dauki kalar wankA(😂) Can cikin bacin su take jin dan muryar mahaifiyarsu kadan kadan tana fadin" to me na na yi maka yanzu kuma? A hankali muryar mahaifinsu ke fadin" du abinda kike shuka min a gaban idannuwan yayana ina kawar da kai ne dan a yanzu sun girma sun kawo mizanin rike du abinda muke aikatawa, idan har na biye maki zamu dawo ne muna raba masu abin kunya , ki sani du talaucina , munina kamar yanda kike fadi ina da galihu, nima mutun ne, ba tsananin soyayarki bane ya saka na kasa daukan mataki a kanki sai dan idannuwan yayana kawai, domin ina jin kunyar daya cikinsu ta bude ido ta ga na aikata abinda zai bata kunya shi ya sa nake fama da karfina nake neman abincin bakina da na iyalina dan gobe kar a zage su, ko yau na mutu bani da bashin kowa a kaina sannan ba wanda zai jefe ni da kalmar na taba cutar sa, na iya talaucina, yanzu tun muna mu biyu ki sanar min inda kika samo makudan kudin da kika yiwa yaran nan wannan siyayar domin dai ni a sanina danginki har yanzu basu gama sake maki ba bale su baki , ke kuwa sana.ar mai kike? Banda kawaye da kika tara wa.inda suka fi kargin mu.amalarku? Ki sanar min , idan kuwa ba haka ba kin ji na rantse ba zasu yi anfani fa suturun nan ba koda kuwa sune zasu daura auren ( domin ta cewa baba wajen aure zasu tafi) Du irin taurin kan mahifiyar su rauda idan mijinta ya juye mata tana shakarsa domin kuwa mutun ne mai hakuri bai iya fushi ba Cikin sanyin murya ta ce" aunty salma ce ta kawo masu tun tafiyarta dubai da mijinta, da ta bani sai na ce ta ajiye min domin idan na kawo masu tun a lokacin zasu iya sakawa ne su je makaranta , ga kayan kuwa masu kyau ne , shine yanzu da suka fada min maganar tafiya wajen auren nan na je na karbo A yanda ta yi maganar sosai ya shagaltar da baba, har ya tino masa zamanin da idan magana ne ba zaka ji muryarta a dage ba, shi ya sani yau da gobe da zugar mutane ne ya sa tun bata damu ba, tun bata kulawa har ta dawo ta fara kulawa cike da mutuwar jiki ya daina fadan, ya jima yana kalonta sannan cikin sanyin murya ya ce" *shin mai ya sauya maki dabi.unki kyawawa wa.inda suka saka nayi maki lakabi da mar.atun saliha? Mugayen kawaye ne suka yi tasiri a kanki ko ke kanki ce kika raina inda kike? Ummu Rauda Allah ya ganar da ke* Yana gama fada ya fito ya bar mata dakin da wannan tsohon daren Jinginar da bayanta ta yi a jikin bangon dakin, a hankali ta sulale kasa tana sharar hawaye, murya kasa kasa ta ce" laifinka ne, komai na zama laifinka ne, ai ba mai son wahala, sai da aka yi maka tayin sana.a ka zo dan girman kai ka nuna aa kai ba zaka yi ba, ba ruwanka da irin damuwar da muke ciki kai dai kanka kawai ka sani , kai a tunaninka a haka zaka aurar da yaya yan mata har biyu? *Ai dole na kara baiwa dangina hakiri kan irin kuskuren da na tafka a baya domin a yanzu da na kuma samun gardin jar miya ba zan dawo na rungumeka mu kare da karnin rana ba* ! A hankali Rauda ta shafa adu.a ta koma ta konta, ita kam dan bata da yanda zata yi ne domin sam tafiyar nan bata yi mata ba ! Cike da adu.ar daidaituwar tsakanin iyayenta ta yi baci Tun karfe tara wayar Aisha take ringin da sauri ta fito ta daga amina ce take shaida mata tafa yi sauri ta shirya Cikin gagawa take kara kyalkyale fuskarta tana duban Rauda wace ke shiri cikin nutsuwa , a dan hasale ta ce" yanzu lalana dan zaki rakani ne kike komai cikin sanyin nan? Ki daga kafa kinga dai birthday din nan na surprise ne, kuma an ce karfe goma yake farkawa daga baci ya motsa jikin minti ashirin kafin ya fito kin ga ki daga kafa kar a yi banda mu Bata bata amsa ba sai tsaki da ta ja cikin ranta ta saka rigarta doguwa mai ruwan peak color , riga ce da ta sha adon duwatsu farare karkarkar kananuwa tun daga wuyanta har kasa an bi an yayarfa masa duwatsun wanda hakan ya karawa rigar kala , sai banban mayafi domin irin rigar larabawan nan ce masu mayafi da kyan fasali da tsada yayar Mahaifiyar su Rauda ta yi masu tsaraba da yayanta Rigunan kala bibiyu ne bakake biyu sai blue da peak Aisha ta dauki baka guda da blue ita kuwa ta dauki peak din da bakar Bata yi kwaliyar komai ba sai yar hoda da ta murza kadan sai jan baki pink sai ta dan furta kwali a idannuwanta Gashin kanta ta kama ta tufke a bayan kanta ta saka ribom dinta fari ta daure sannan ta dauko mayafin ta gyara shi ta ninka shi yanda zai yi mata dadin dauri sannan ta daidaita ta dora shi a kanta ta yane kanta da shi ya kasance ya rufe mata gashin kanta sai yayi irin yanda larabawa suke Sosai wannan riguna suka karbi jikin su Rauda, domin daga sama sun dan matse daga bakin kugu suka bude sai hakan ya hau da yannayin tsarin halitar jikinsu wato coca cola Kiran amina na ba adadi ya saka Aisha wartan pos ta fice tana fadin idan kika dora wasu mintunan zan yi tafiyata A haka itama ta fito, bakin takalmi ne a kafarta mai dan tudu kadan Sun yi tafiyar a kallah minti talatin kafin suke shigowa anguwar gra Kofar wani gida suka ja suka tsaya Dane horn Amina ta yi wanda hakan ya baiwa masu gadin kofar damar jin da mai son shigowa Daya daga cikinsu ne ya fito ya karaso wajen motar ya ja ya tsaya A hankali Amina ta sauke gilashin motar tana kallonsa Fuskarsa a hade ya ce" takardar shedar ke yar familly din ce Baki sake suke kallonsa, Amina ta ce" ko dai mun yi batan kai ne, shin ba nan ne gidan su *Hafsa* ba? Bai saki fuskarsa ba yace " eh, aman dokar mai gidan ce idan dai kai ba na gidan bane baka da carte din shedar kai dan gidan ne sai ka yi kiran number oga yayi kiran mu ya bamu izinin ka shigo da mota idan ba haka ba kiwa sai dai ka shiga a kafa koda kai wanene idan kin kula ga motoci nan na kawayen madame domin abinda take shiryawa bata so oga ya sani Cike da mamaki Rauda ke binsa da kalo garjejen kato wanda ko jayaya ba zaka so yi da shi ba, kofa maganar ne zaka yi gudun yi da shi Ajiyar zuciya ta sauke da ta ji Amina na koda wannan tsarin tana fadin" lale dole ne manya manya ne bara mu fito, ta juyo wajen Aisha da ta fara yin la.asar tace" kawata mu tafi ko Haka suka bar motar suka fito, Amina ma doguwar rigar ce ta saka red color sai dai tata ta dameta sosai sai ta yafa mayafinta a saman kanta Haka suka shiga wannan gidan wanda kallo sai ka shigo idannuwanka zasu baka kalaci domin gida ne mai girman gaske , faduwar tsaruwarsa ba zai yiyu sai dai nace ya hadu iya haduwa ko a kasar waje sai haka Suna shiga suka tarar da wata mata da uniform na ma.aikata cikin sakin fuska ta tambaye su wajen birthday suka zo Suka bata amsa da eh, nan ta nuna masu wata hanya da kofa a jikinta ta ce" ga bangaren Ogan nan Kallon juna suka yi suka nufi hanyar inda Rauda ke biye da su a baya kamar kwai ya fashe mata a ciki domin gaba daya ji take tamkar bata da laka A tare suka furta waouh!!! Domin tsarin wannan waje ya zarce wanda suka baro, tsari ne irin na turawa domin kasan shinfide yake da gazon wato wannan tsanwar ciyawar irin ta filin ball mai laushi a kafa da santsin takawa Sai wasu dogayen shukar dabino a jejefe a filin A nan filin wajen motsa jiki yake an kawata shi fa dukan abubuwan bukata na motsa jiki, da wani dan karamin frij mai cike da dukan abin sanyi wanda bayan ka gama motsa jikin zaka dauka ka fitar da kishirwa Gefen dama kuwa wasu fararen kujerun karfe ne irin wa.ina ake sakawa daga cikin kasa, sai dan nesa da su abin lilo ne shima an yi masa fenti da fari sosai ya hasku a kan wannan ciyayin Sai wani dan table da runfa a samansa gefensa kuwa wani dan sip ne cike da litatafai na adini da na turawa Wata sansanyar iska ce ke kadowa tana badawa dalilin ruwa da ake baiwa wannan ciyayi da kuma shukokin nan sai ya kasance wajen ya zama gurin samun nutsuwar du wani bawa mai cikakiyar lafiya Wajen mutanen da suka hanga a tsatsaye suna daukan hotuna du yan mata sai yan gidan da basu fi su biyar ba gaba daya dai har su Rauda ba zasu kai su 15 ba Gaisawa suke da hafsa wanda Rauda ta raja.a a shakar kanshin wajen somin kanshin shuka yake bayarwa da sanyi mai dadi Hello???????? Hafsa ta maimaita a karo na biyu domun tana yiwa Rauda sanu da zuwa aman bata ji ba Da sauri ta juyo da fuskarta, kunyar hakan ya saka ta sakin murmushi wanda ya baiwa fuskarta damar lotsawa sosai Zaro ido Hafsa ta yi ta ce" waouh, masha Allah freind wannan ma kawarki ce? Ta fada tana tambayar Amina Amina ta ce" kanwar kawata ce baki ga suna gama ba? Hafsa ta ce" eh gaskiya akoy kama, da farin fatar sai dai wannan ta fi yayar nata manyan idannu da kuma dimple masha Allah, ina son abin nan Murmushi suka yi gaba dayansu wanda a daidai wannan lokacin murmushin kan fuskar su Aisha, Rauda, Amina, da sauran jama.ar da suka zo a matsayin gaya sanadiyar razannan kyan bayan Allahn da ya bayana a gabansu da shigar yan ballllllllllll 🙆🏽 to fa kar Hafsa maimakun ta birge a samu matsala domin dai Yayanta koda yana mugun sonta a matsayinta na auta sai dai ustaz ne irin mai mugun ustazacin nan...... *❣IDAN KA RAINA INDA KAKE❣* 5⃣ Na : *SAJIDA* Murmushi suka yi gaba dayansu wanda a daidai wannan lokacin murmushin kan fuskar su Aisha, Rauda , Amina da sauran mutanen dake wajen a matsayin wa.inda aka gayata ya dauke sakamakon razanannan kyan bawan Allahn da ya bayana a gabansu da shigar yan ball Bakar riga ce a jikinsa mai gajeran hannaye iya damtse, rigar a lafe take a jikinsa ta kama fafadan kirjinsa , ta rike damatsunan hannunsa kam sannan ta bada damar gannin yannayin girman kafadunsa Sai wando baki wanda ya dan zarce gwuiwa , ta dan rike kafar daga kasa, Da yake ya fito ne dan ya motsa jiki bai fito da hirami ba domin shi mutun ne ma.abocin saka hirami, a kashi dari na suturun da yake sakawa kashi casa.in na kayan larabawa ne hakan ya saka ba kowa ya san cewa kansa lulube yake da ni.imtacen gashi konce baki sidik mai laushi da kyan gani ba, sannan shi mutun ne mai matukar kunyar a ga jikinsa, ya kasance yana da wani kazamin kishi wanda shi kansa yana kishi kansa domin sam baya bari a ga yannayin halitarsa shi ya sa du inda gidansa yake toh fa da wajen motsa jiki wanda ya kawata shi da komai domin a nan yake zuwa ya saki jikinsa ya motsa jikinsa ya buga ball yanda ya kamata Jin alamar mutane a gudansa ya saka shi juyowa da sauri wanda yayi daidai da bugawar zuciyar du wanda yake ba muharaminsa a wajen ba Mutsuke idannuwansa yake cike da mamakin gannin jama.ar wajen, nan fa yannayin shigarsa ya fado masa a ransa yayi gagawar kallon jikinsa ya kuma dagowa dan kuma shaida cewar wai su waye ma sannan mai suke masa a wajen nan???? Da sauri Hafsa ta tarbo masu katon cake din da ta saka aka yi mata masu aiki biyu suka gunguro si a kan table mai tayoyi An mugun kawata wannan cake sannan daga gefe gefe an yi rubutu Da sauri ta karasa kusa ta shi ta saka hannunta a tafin hannunsa ta jawo shi wanda ya zame mata tamkar mutun mutuni wanda hakan ya hana shi nuna dadin rai yake ciki ko akasin haka, shi fa kwatakwata bai fahimci inda Hafsa ta dosa ba, mutanen nan su waye? Mata, sannan du yan mata cikaku, mai suke nema a nan? Kallon mai suka tsareshi da shi?? *SURPRISE* Cewar Hafsa tana mai nuna masa cake wanda a tare suka kalo wajen cake din da aka rubuta da farin cream *HAPPY BIRTHDAY YAYA SUDAÏSS* Sai a wannan lokacin ya tuna cewar yau zagayowar ranar haihuwarsa ce, Hannunsa na dama ya dago ya dafe kansa da shi, daidai wannan lokacin Rauda ta sada kanta kasa domin da ta kallo fuskarsa gabanta faduwa yake, daman akoy bahaushe da irin wannan halita? Ya salam ya furta da muryarsa wace ta fito a muryar kato sak, domin bata da laushi ko kadan irin muryar sadaukan maza kenan muryar dake fadar da gaban mutane, muryar dake tsoratar da maza sannan ta hautsina tunanin yan mata.... Hannunta da ta riko shi dan ya je ya yanka cake din ya bi da kallo, sannan ya dago fuskarsa wanda ta fasara labarin zuciyarsa domin kuwa ya mugun hade fuskar ya bayanar da bacin ransa Fizge hannun nasa ya yi ya wurga mata jajayen idannuwansa , a hankali ya taka har zuwa gabansu, ya fice cake din ya tsaya kikam a gabansu Kudirin da ya saka shi yin hakan , ya so ya tafka masu rashin mutunci domin a ganinsa gaba dayansu ba yayan mutuncin bane tunda har suka iya fitowa a fidajen su cikin kwaliya da niyar zuwa birthday din namiji, namijin ma wanda basu sani ba, zuciyarsa ta yanke masa hukuncin ai suma yara kananu da su sun san su talata kansu wa shi Tun daga yan matan hudu ya fara fuskarsa a hade wanda hakan ya saka su kyarmar tsoro dan basu san laifin da suka aikata ba abin alkhairi na neman zame masu matsala Kallon kyama yake binsu da shi har ya zo wajen su Amina wace sai dan murmushi take saki Kallo daya yayi mata ya ja tsaki domin kara turo kirji take tamkar wata yar bariki, Tsakin da ya ja ne ya saka Rauda saurin dago da kanta suka Cikin rashin sa.a idannuwansu suka sarke da juna wanda a tare zuciyoyinsu suka buga Saurin rintse idannuwansa yayi ita kuwa ta mayar da kanta kasa yayi saurin kawar da fuskarsa a fuskarta ya kalo Aisha Aisha da ta yi mutuwar tsaye tun lokacin da idannuwanta suka yi arba da shi, wata irin zazafar kaunarsa ta darsun mata a zuciya, hankalinta in yayi dubu to ya tashi a wannan lokaci sai abinda ya kuma tayar mata da hankali shine irin kallon kyamar da ya bisu da shi Ba tare da ya furta uffan ba ya juya yana takunsa na kakarfan namiji ya shige tare da turo kofar da karfi Da sauri Hafsa ta dora hannayenta a kai ta ce" na shiga ukuna, daman granny ta fada min na fada masa ya shirya kar na yi surprises dinsa na yi mata gardamar cewa dadi zai ji🙆🏽, ya salam, yanzu ya zan yi yayana yayi fushi sosai domin yana yi min uzuri a kan sauran mutanen gidanmu da tuni ya hukunta ni Husna ta sauke ajiyar zuciya ta ce" baki ga tunda ya fito jinina yake hawa ba? To kinga tafiyata dan ba zan taba manta marin da yayi ba sai da dan kunena ya cire sannan na saki fitsari da girman nan nawa dan kawai na dauko masa ruwa ban duka ba na bashi a tsaye dalilin mantawa da nayi da dokarsa ta a duka idan za.a bashi abu, ai ni yama yi sanyi nake gani yanzun domin kina gani baifa daki kowa ba dan haka tun muna shaida juna ku fice mu tafi Jin haka ya saka gaban amina ya fadi, ta juya tana kallon husna, Husna cousint dinsu ce, a komai ta fi amina kyau din , kudin kai komai ma aman tana tsoronsa haka? Ita fa tana son mutun mai irin kirar sa da kyansa da kudinsa aman bata son namiji masifafe, tana matukar tsoron masifarsa aman zata gwada idan har zai daina sai ta aure shi 🤔🤔🤔🤔 Suna sauri suka fito gaba dayansu, kowace ta kara tsorata da rashin maganarsa kowace tana tafe ne tana waigen bayanta domin shirunsa yafi fadansa tayar masu da hankali Wayar hafsa ce ta yi kara ta daga ta yi tsam tana sauraro sai can ta sauke ajiyar zuciya ta juyo wajensu murya a raunane ta ce" kawayena, ran yayana yayi matukar baci hakan ya sa ya saka a hana kowace daukan motar ta har sai ya waiwaye ku Gaba daya hankulansu ya kara tashi du suka kali juna, Amina ta ce" ki rufa min asiri Hafsat, idan na koma gida ba motar momyna zata yi min duka ne domin sai da ta gargade ni kar na lalata mata mota, to na je nace mata me ma wai? Gaba dayansu ba wace ta yarda zata tafi ba motarta banda su Rauda da suka yi shiru kawai suna bin mutanen wajen da kallo kowace da damuwarta daskare a zuciyarta Ajiyar zuciya Hafsa ta sauke ta ce" to abinda nake so da ku, ku mu je wajen Granny Daya daga cikinsu ta ce" hafsy, daman kin san yayanki bashi da mutunci kika gayace mu ? Me yasa kikai mana wannan wulakancin? Hafsa ta juyo ta dan hade rai ta ce" aman Ramlat baki iya magana ba ko? Kin san ko wanene kike hada shi da rashin mutunci? Wannan da kika gani tamkar mahaifinmu yake, haihuwarmu ne kawai yaya Sudais bai ba! Dan haka ko mai yayi ba zan taba yarda wani mahaluki ya zage shi ko ya so fada masa maganar banza, ba gori ba ki dubi girman gidannan ke kin san koda bayar da motarki yayi idan ya tashi baki wata sai ta ninka taki a komai, hukunta ni ne zai yi ta wannan hanyar dan haka ki kiyaye Ta karashe tana kara hade rai Amina kali Aisha wacr har wani gumi ke tsatsafo mata a fuskarta ta ce" kawas kin ga yanda birthday din ya koma, zaku iya jira har a bamu motar ko kuwa tafiya zaku yi? Da sauri Raudat ta ce" aa zamu tafi Baba yace kar mu yi yama , kin ga bamu san lokacin da zai hakura ba kar a yi mana fada Amina ta tabe baki bata ce komai ba Hafsat ta ce" ohk aman ku da kuka zo tare yanzu ai ba zaku shiga motar haya ba ko? Kun ga yanda yayana yaki jikin ya ga mace a cikin motar haya cakule da maza sai haka kawai yayi ta fada tamkar ya santa Amina ta ce" basu da ita Ne motar! Cike da mamaki Hafsat ta kalo wajen su Rauda, suturar jikinsu ta karyata abinda Amina ta fada a zuciyarta aman duda haka sai ta ce" kai freind hali dai yana nan, ki kali yannayin shigarsu ai suturar jikinsu zata sayi hudun taki domin wannan a wani shago a abuja na ga irinsu Cike da jin haushin maganar hafsa amina ta ce" eh haka nima na yi mamaki , aman kuma basu da ita , ko keke basu da shi bale mota ke fa komai basu da shi.... kin san anguwarsu ne ? Yan anguwar...... *YA ISA* ! Rauda ta fada cike da bacin rai domin sun kaita bango, tun farko ranta ke jagule da irin kallon wulakacin da wannan wulakantacen yayan nata ya yi masu ya gama bata mata rai sannan a zo nan ana cicirasu daga cewa zasu tafi sai a kama fede su haka? Cike da bacin rai ta yi masu kalon sama da kasa , a gaskiya itama ta san hafsa ta hadu dan haka ta juyo wajen Aminar ta ce" eh gaskiya kika fada bamu da komai, mu ba kowa bane , bamu da ko keke ke naira dubu ta fi karfin kaf yan gidanmu bale mu! Sai dai da ace ke mai ilimi da kafin ki yi wannan maganar sai kin karewa *Halitar dukan mutanen dake wajen nan*, kin ga ai wata ta fi wata ta wani fannin wata ta fi wata ta wani, sai ki shaida *Allahn* kennan, wanda ya baki kudi ni kuwa nima ya bani arziki mai tarin yawa wanda na fi ki da shi , ta karashe tare Da kuro idonta farin ya haske su ta juyo wajen yayarta wace ta zama wata iriya ta ce" ai kin ga irinta, da ace kin barni a gida cikin mutuncina da ban yi doguwar tafiya marar anfani na tare a wajen da ba.a san darajar Dan adam ba, Fuuu ta kama hannun Aisha tana janta ita kuwa tana biye da ita tamkar kwai ya fashe mata a ciki Da sauri Hafsa ta bi bayansu tana fadin" i.m so sorry plz, ni tambaya kawai na yi Rauda ta juyo ta ce" ni kuma amsa na baki Hafsa Hafsa ta yi murmushi ta mikowa Rauda hannu ta ce" ki yi hakuri Rauda ta sauke ajiyar zuciya ta mika mata itama sukai musabaha sannan ta rako su har wajen gate sukai salama har ta nemi lambar Rauda ta shaida mata bata da waya Cike da mamaki ta juya , rana mamakin a irin kyan rauda aman bata da waya , lale ba irin yan matan zamani bace domin kuwa da irin wasu yan matan ce da ta mayar da baiwar kyan da allah yayi mata wa *JARINTA* Haka suka fito suna tafiya a kafa, gashi wajen da mugun nisa kafin a iso bakin titi, baban tashin hankalin ma basu wani fito da kudi ba dan ba wace ta yi tunanin hakan zai kasance Rauda tana dan gaba da Aisha domin tamkar an zare mata laka take tafiyar, Can kamar an tsikareta ta kai kasa ta duke ta dora hannayenta bibiyu a saman kanta ta fasa wani uban ihu da kuka mai firgitarwa wanda ya saka rauda mugun faduwar gaba ta juyo da gudugudu ta karaso wajenta ta duka daidai da ita ta kama hannayenta tana tambayarta abinda ke damunta Aunty Aishana, dan girman Allah ki yi hakuri in dai dan wulakancin da suka yi mana ne ai kin ga na rama mana ko? Ki yi hakuri da kukan nan haka kar zuciyata ta buga Aunty dan Allah ki tashi mu yi tafiyarmu ki yi hakuri haka;;;; Rauda ta karashe tana mai matsar kwalah Aisha kuka harda majina ta sauko hannunta daya ta dora saitin zuciyarta, ta rintse ìdo muryarta na crac..........k.........in..........g ta ce" Walahi *INA SON SHI*!!!!!!!!!! *READER SHIN KUNA FAHIMTAN RUBUTUNAN KUWA? KUN GANE INDA NA DOSA?* Shin Wanene Aisha ke so??? *❣IDAN KA RAINA INDA KAKE❣* 6⃣ Na : *SAJIDA* Tamkar zarara take acting, ta damko hanayen Rauda ta dora saman kirjinta cikin muryar kuka ta ce" kina jin yanda zuciyata ke bugawa? Kina jin yanda nake ji kuwa? Zuciyana fitowa zai yi daga gangar jikina, ki taimake ni, koda baya sona ni ina son sa koda zai yanka namana ne ya aureni Bata san dalili ba, itama sai ji ta yi hawaye na bin kuncinta, sannan daidai da bugun zuciyarta ya canza irin ta tsorata da kalaman yayarta bayan hakan bai dace ya wani firgitata ba domin kuwa hakan ba abin mamaki bane idan ya fito daga Aisha Cike da tsoro ta share hawayen da ya zubo mata, ta tataro nutsuwar dole ta dorawa kanta ta kama kafadun Aisha da dukan hannayenta ta tausasa murya ta ce" ki yawaita karanta innalilahi wa ina ilaihi raj.une , a bayane ko a boye a cikin zuciyarki, hakan zai saka ki ji sanyi Tamkar wata yarinya karama ta dora kanta a saman kafadar Rauda tana sauke ajiyar zuciyar kukan fa ta sha Shatttt mota guda uku bakake suka zo suka fice da gudun tsiya wanda ya saka Rauda saukin dago da kanta cike da jin haushi ta cire takalmin kafarta ta jefi motocin ranta bace domin dai da gabanta ya fadi daman tana cikin zulumin halin da yayarta ke ciki! Tana ta lalamin Aisha ta mike su tafi motocin nan suka dawo a layansu irin na dazu A tare suka dago da kansu dan gannin ko su waye haka Lafe yake a bayan motar, ya zabga masu harara daidai fadiwar gabansu a tare Raudat ta dago da yatsarta guda ta nuno wajen motar domin sai da yayi hararar kamaninsa suka fado mata, tabas shine mutumen da ya harareta wajen danja! Kwarai kuwa shi ne shi ne! Takalmin da ta jefa masa ya bude glas din motar, hannunsa saye yake cikin gan ruwan kasa, kansa da hirami sai daukar ido yake ya mayar da wutsuyoyin bayan kansa Fuskarsa cike da alamun kyankyami ya wurgo mata da takalmin suka juya bayan sun tada masu kura suka tafi Wannan karron ba Raudat ce ke jan hannun aisha ba, Aishar ce ke jan hannunta cikin wani irin yannayi ta tsayar da mai adaidaita kafar Raudat guda ko takalmi babu domin sam bata saurareta ta saka takalmi ba Suna karasowa ta sauka ta fada gida, Rauda ta nemi alfarmar yayi hakuri ta kawo masa kudinsa Tamkar an yiwa Aisha mutuwa ta tarar da ita tana fadawa mamansu tana rusa kuka Kudin mai napep ta dauka ta kai masa ta juyo ta shige dakinsu ta konta ta lumshe idannuwanta inda take jin muryar Aisha na fadin" wa gare mu umah? Mai gare mu,? Ko keke bamu da shi, bamu da fada a ji koda a kauye ne bale a cikin gari, Umah ta yaya zai so ni? Ta ina zan bi ya so ni? Shafa kanta magaifiyarta ke yi, cikin sanyin murya ta ce' ba kin ce ELHAJ SUDAIS MALALE BA? Aisha ta daga kanta Mahaifiyarsu ta ce" in dai shi ne, banban dan kasuwa, yaron da yayi rantsuwar ba zai taba kasancewa kalkashin wani ba yaron da ya san kan nema, tabas shine dan gidan Omar faruk Malale tsohon ma.aikacin gwomnati wanda dalilin wani wulakanci da aka taba yiwa mahaifinsa lokacin ya taso sosai yayi rantsuwar ba zai kasance karkashin wani ba Aisha ta dago cike da mamaki ta ce" umah a ina kika san labarinsa, ? Kin kuwa gane da wa nake magana? To ya aka yi kika fahimci cewar da shi nake bayan ni ba hotonsa na gwada maki ba, sunansa kawai na fada maki sai kwatancen gidansu da kadan daga cikin dabi.unsa aman har kika gane? Umah wannan fa da ganni mahaifinsa wani gagarumin mai kudi ne domin jikinsa bai san wahala ba, bai taba saninta ba , Daidai wannan lokacin Hafsa dake kallon Kawarta Amina wace ta wuni a gidansu har dare na kokarin yi, take shaidawa Hafsa cewar itafa zaman jiran nan da take harda soyayar yayanta a zuciyarta, da a ce zai so ta da ta more rayuwarta Murmushi hafsa ta yi ta ce" ni ba zan hana ki ba, domin ban san ko ke zaki zamo ta farkon zabinsa, aman abu daya zan iya fada maki shi ne yayana yana da *aure* iyalinsa na saudiya domin yafi jin dadin zaman kasar fiye da ko.ina a duniya Amina gabanta ya fadi" ta furta yana da aure fa kika ce? Aman shine yake tare da lafiya haka ? Cike da mamaki hafsa take kallonta ta ce" ban fahimci yake cike da lafiya ba? Amina ta sauke ajiyar zuciya ta ce" to ai abin ne, na ga mafi yawancin masu auren nan zakina ganninsu tamkar a firgice suke, ko me yasa haka oho?? Hafsa ta yi murmushin shirmen Amina, ta ce" ni kam ban taba irin wannan luran ba, abinda ma na lura da shine idan ka yi aure ai ka zama cikaken mutun , nutsuwa da konciyar hankali na tabatuwa a gare ga, bale idan ka yi dace da abokin rayuwa nagartace Amina ta ce" kin ga kawata mu bar maganar nan, dan kuwa a yanzu na tabata ya fi karfina Bayan Hafsa ta raka Amina ta dawo ta je wajen kakarta ta zauna suna hirarsu cikin nishadi Can ta nisa ta ce" granny, kin ga wannan kawar tawa da na raka ta karshe cewa ta yi tana son yaya, Karkar hafsa ta yi tsam can ta yi murmushi ta ce" Hafsa, wai kina nufin uban gida? Aa ai ba zai taba son yarinyar da ta kale shi ta fara sonsa ba, ba zai so yarinyar da take irin shigar wannan ba, ba zai kaunaci yarinyar da zata iya take kunyarta har haka ta bayana abinda ke ranta ba domin kuwa shi din wani mutun ne mai wasu irin halaya, komai nasa yana son ya kasance special.....baya son abinda kowa ya sani ....... *Wanene Sudais?* *SUDAIS* ya kasance jikan Ramatu da Saidu, dan Muhammad da Fadima, kanin Bilkissu sai marigaya Shafa, Rafi.a, yayan *Hafsa* Muhamad ya kasance tsohon malamin makarantar boko secondary shi da matarsa Fadima Da wannan aiki suke rufawa kansu asiri harma su dan taimaki dangi Tabas arziki basu gade shi ba, basu da shi basu da dalilinsa domin wannan aiki nasu gaba daya albashin nasu bai taka kara ya karya ba Bayan aurensu shekara na zagayowa Fadima ta haihu ta samu yarta mace mai shegen kyau aka saka mata bilkissu, tun daga nan sai haihuwar ta kasance mata tamkar riritsa, shegara na zagayo ta sake haihuwar Shafa, sai Bilkissu Sai *SUDAIS* Yayansu sun taso cikin rufin asiri da konciyar hankali, kafin mai faruwa ya faru Sudais ya taso da wani irin hali wanda dalilin haka mahaifiyarsa ta yi ta shiga asibiti domin kuwa sai da ya kai shekara biyu kafin ya fara dan cicira magana, da farko sun yi tunanin ko kurma ne? A shekara hudu ta kan zaunar da shi ne gaban dan karamin akwatin tvn su ta kamo masa tashar larabawa domin a abinda ta lura yana kaunar irin tashohin dan ya fi zama ya barta ta yi ayukan gabanta idan ta kuna masan Shekarunsa na karuwa ne maganar bakinsa ta fito ra Idan ka kali halitar Sudais ya dauko kamanin kakan mahaifiyarsa domin buzun mutun ne kakarfa irin tsofafin rebel din nan na can cikin garin Timiya dake wajen Agadez, mutun ne dogo sambal, duda ya kai tsufa fata du ta yakune abinka da farin mutun mai nuna tsufa, aman da ka kale shi zaka ga cewar wannan ba karamin basamuden mutun bane, sannan har ya mutu ba zaka ce ga inda ka ganshi zaune ba rawani ba ko yayansa na cikinsa ba zasu shaida irin ranar nan ba sai matarsa wace ta kasance sirinsa ta biyu Sanadiyar auren mahaifiyar Fadima ya zubar da makaman yakinsa dalilin mahaifinta da ya kasance tsohon malami shi ya nusar da shi ya bashi auren yarsa bisa salatin annabi Muhammad sallalahu alaihi wa salam a matsayin sadaki Kakan Sudais mai sunna *KULLEY* har ya mutu damatsunan hannunsa basu sauka ba domin halitarsa ce haka ba wai da karfi ya mayar da jikinsa haka ba, Mutun ne dirare, tsayaye, gashin kansa kuwa har kitse masa mahaifiyar Fadima ke yi (paix a ton ame grand pere Kulley🤧) Wani lokaci Sudais ya zarce shekara goma suna zaune da mahaifansa ya kali mahaifinsa ya ce" Aba, ina son shigar larabawa, Aba zaka kai ni kasar latabawa na rayu a can? Wannan magana ta daki zuciyar Muhammad mahaifin Sudai, domin sudais bai taba nuna bukatarsa a komai ba, bai taba nuna so ko kin abu ba asalima bai taba nuna yanada sha.awar rayuwar kanta ba sai dai yakan kure balaraben da ya gani da shigar larabawa harma ka ga alamar yana sakin murmushi Abansa bai iya furta masa kalma daya ba sai mamansa ta kamo hannunsa ta ce" Sudais, ka yi ta adu.a Allah ya yasare mana ta hanyar da bama zato bama tsanmani ka ga sai Aba ya kaika Kasar larabawa , wai shin ya akayi kake son kasar larabawa? Ya dago da kansa ya ce" momy dan fiyayen halita balarabe ne, sannan a shigar larabawa daga ta matan har ta mazan ta kasance kamilaliyar shiga, kin ga a tv ko idan mun tafi masalaci da Aba zaki gansu ne sun saka doguwar jalabiya sun dora hirami, Insha Allah zan kasance mai yin irin shigarsu idan Aba ya saya min Murmushi ta saki, ta dago tana kallon mijinta dan ta basar da yannayin da yake ciki ta ce" ka san wani abu kuwa ABU SUDAIS? A hankali ya girgiza mata kai, ta ce" idan na kali yannayin Sudais bayan kama da yake da baban cikin gida ( wato mahaifinta) harta yannayinsa ya dauko, duba da shirunsa, da murmushinsa, da kawar da kansa a kan dukan abu koda yana tsananin so, ka ga fa hannayensa yanda suke mulmulewa Murmushi Muhammad yayi ya ce" *SADAUKINA* Allah ya raya Uban gida Daga nan suka ware suka ci gaba da hirarsu, aman tun daga lokacin du wata idan ya dauki albashi yakan siyowa Sudais jalabiyoyi farare karkar masu karamin kudi da samon hirami tun daga lokacin yannayin shigarsa kennan Rayuwa na juyawa, tafiya na kara nisa, a cikin shelaru biyar da suka karu an samu ci gaba an samu jin dadi an samu mace mace ciki harda mahaifin Fadima, sannan an saka auren yan mata ukun nan cikin ikon Allah Allah ya fitar masu da miji a tatare wanda da mai shekara goma sha biyar rafi.at, da mai shekara goma sha shida Shafa, sai mai shekara goma sha takwas Bilkissu kowace ta samu mijinta mai mutunci har an saka rana Bakar rana wace ta zo masu da canje canjen rayuwa ta sanadiyar zamowar Sudais zakara Aure na sauran kwana biyu , sai shirye shirye ake... daidai karfinsu sun ciru sun kulu sun yiwa yayansu kayan daki daidai gwargwadon iyawarsu A ranar juma.ar nan suna farkawa Gaba dayansu sun tashi da wani irin yannayi, gidansu kuwa har ya fara cika da dangi da aminan arziki Rafi.at ce tsugene kusan mahaifiyarsu, ta ce" umana yau baki saka mana albarkar ba fa Fadimatu ta dago ta yi murmushi ta dan jawo kuncinta ta ce" ai yau du sai na tashi da mutuwar jiki Rafi.at, a kulun nakan saka maku albarka safe da yama, Allah yayi maku Albarka ya yafe maku kurakuranku na jiya da yau da safe da wanda zaku yi nan gaba, Murmushi ta yi ta ce" umanmu yau zamu tafi Haka kawai ta ji gabanta ya fadi da maganar rafi.at ta ce" ina?? Rafi.at ta ce" ummah fa, wajen aunty? Da ta ce yau ya kamata mu je mu karbo sakon gaba dayanmu har mun shirya aunty bilki ce take ta jan jiki har yanzu Mahaifiyarsu ta yi murmushi ta ce" ai fa sarkin nawa, ita kam akoy sanyin jiki ai Suna tsaka da maganar Shafa ta fito, haka take daukan ido domin itama ta dauko fatar kakanta sosai ga tsayin gashi har baya, Abaya ce ta saka mai ruwan ash coler sai ta kara haska fatar nata Itama tsugunnawa ta yi suka saka mahaifiyarsu a tsakiya suka ce umah bara mu yi selfi Ai kuwa suka dauki hoto, Suna tsaka da yi sudais ya shigo, da yake gaba dayansu ya fisu tsayi da kakarfan jiki sai ya kasance shine karami aman suna shayinsa, gashi ba sake masu yake ba Rafi.at ce ta yi kalar tausayi ta ce" broh ka zo mu yi hoto plz Haka kawai ya ji yana son yayi hoton dan haka ya shiga suka yi su hudun Wayar Shafa ce ta dauki kara ta daga , bayan ta kashe ta ce" umah mu tafiya zamu yi, kinga sai gagawa ake aman mu muna nan kar su tafi ba.a bamu sakon ba zamu karbo mata nata kawai Mikewa ta yi tana wani irin sauki ta kama hannun Rafi.at ta ja da wani irin karfi na mamaki tana fadin mu tafi.... Fadimatu tana fadin" baku karbi kudin napep din ba fa aman ina har sun fita kofa Da sauri ta mike tana fadin" ka ga sudais zo ka karba ka kai masu Shima mikewa yayi ya bi bayan mahaifiyarsa sai dai me, suna shiga dakin ya ga ta yi wani irin tsayawa ta dafe kirjinta, da sauri ta juyo tana kallon kofar dakin nata Cikin azama ya karasa yana riketa ya ce" momy, lafiya? Ko kirjin naki ne? A hankali ta sakar masa nauyin jikinta domin a lokacin ji take tamkar ana zare mata laka gaba daya, Bakinta ta bude zata yi magana sai dai ji ta yi an fasa kuka ana faman kiran inalilahi wa inna ilaihi raj.une A hankali ta lumshe idannuwanta sai hawaye suka biyo baya, wani irin karfi ne ya zo mata ta mike ta bi bayan Sudais da yayi gagawar fita dan gannin menene ake shigowa da haka? Idannuwansa ya rufe yana mai jin zuciyarsa zata fito daga gangar jikinsa sanadiyar arba da yayi da abinda ake shigowa aka dora saman tabarmar da yanzu suka tashi a kai Da sauri ya juyo dan tare mahaifiyarsa sai dai inna, ture shi ta yi ta karasa kusa da mijinta da ta gani ya dukar da kansa ya fasa kuka Tana karasowa ta shiga kifta idannuwanta sakamakon jin da ta fara yi sun fara rufewa, ta fara rasa ganninta Wani irin duhu ne ya rufe idannuwanta sakamakon gannin gawowin yayanta amare biyu cikin jinni a konce basa alamar motsi A hankali ta kai kasa numfashin nata ya dauke gaba daya Daga wannan rana wannan family ya afka a rayuwa mai wuyar fasara, ciwo ya zo ya sarki Mahaifiyarsu, Muhammad ya tsayar da zuwa wajen aiki..., Ciwo yayi ciwo a asibiti aka bukaci dubu dari biyu dan za.a yi mata aiki Hakan ya sa ya dauki Sudais suka je ma.aikatarsu ya samu ogansu Nan yake fada masa rasuwar da bukatarsa na a ranta masa wa.innan makudan kudade zai biya a sannu Kare masa kallo yayi cike da isa ya ce" Wa.inda suka rasu Allah ya jikansu, aman karka manta malan Muhamadu daman muna binka dubu ashirin da muka ranta maka zaka cika ka sayawa yayanka kayan daki, to baka biya wasu ba zamu baka wasu? Gashi ya dace ka dawo bakin aikinka dan ka samu a baka albashinka ka biya mu bashin mu, kai in ba abinka ba Malan Muhamadu shekara nawa ya rage maka ka yi ritaya? Du yawan shekarun ba zasu fi 3 ba, a cikin su zaka iya biyan mu ne? Cike da mamaki ya dago yana kallonsa ya ce" aman dai elhaj du irin shekarun da na bata ina bauta wa wannan makaranta a yau da bugata madaukakoya ta taso min za.a gagara biya min bayan bashi na nema? kai ka san koda aikina ya tsaya sai na biyaka zan iya samun konciyar hankali Dakile fuskarsa yayi ya ce" shin kana da wata sana.a ce bayan wannan? A nan fa ka kare da ni ka dogara malan Muhamadu, sai ka yi min aiki na biyaka kake samun na cin abincin gidanka, to ta ina zaka samu irin haka??? Da sauri Sudais ya dago da kansa a karo na barkatai , wasu hawaye ne masu zafi suka zubo masa ya mike ya kama hannun mahaifinsa ya fito da shi , fuskarsa ya kure da kallo sai ya bude baki zai yi magana sai kawai bakinsa ya kwashi rawa sai ya rufe, idannuwansa sun yi jajir, ya kasa aiwatar da wani abu A hankali mahaifinsa ya dafa kafadarsa ya ce" ka kontar da hankalinka Sudais wannan ai ba komai bane ka ji, ka tashi ka yi jirana Da sauri sudais ya girgizawa mahifinsa kai, ya saka hannunsa a aljihu ya ciro naira dari biyunsu ta keke napep ya dankawa mahaifinsa, murya na rawa ya ce" Ka koma asibiti Aba, Har ya fara taku cikin sauri mahaifinsa ya ce" Sudais ina zaka je ne haka? Ja yayi ya tsaya, ya juyo da sauri ya ce" *ABA, ZAN JE NEMAN INCINA NE DOMIN NI SUDAIS MUHAMMAD NA YI ALKAWARIN BA ZAN YIWA WANI KATO NEMAN KUDI BA* Tun daga wannan rana, *SUDAIS MUHAMMAD* ya fara neman kudi da jarin dubu ashirin da kakarsa ta siyar da gwal dinta na aure wanda mijinta kulley ya bata a tadar auren *buzaye* ta biya kudin aikin yarta sannan sauran aka yi dukan bukatu ciki ta baiiwa sudais dubu ashirin ya ja jari Tabas sudais ya sha wahala, rana ta dake fatarsa , ruwa ya dake shi, sanyi ya kare a kansa.... Gari gari yayi ta bi, kasuwanni yake ci na kauyuka, yana saron yadidika yana kaiwa kauyuka, cikin ikon allah kasuwar kara daukaka take, haka ya shiga harkar wayoyi yakan sari kananuwan wayoyi ya siyar har ya fara manyan wayoyi abinda da dukan wanda Allah ya nufa zai yi arziki tofa ko mai ya taba zai yi albarka ne A haka ya Allah ya dafa masa, ya kasance yana samun daukaka, lungu lungu ba inda kafarsa bata shiga dan neman ci gaba A cikin shekara goma da suka karu Mahaifiyarsa ta kara samun haihuwar ya mace aka saka mata *Hafsat* wace yake jinta tamkar nama daya a miya, sannan kudi dai mai sunnan kudi Sudais ya fara tara shi sannan halitar jikinsa tana kara bayana kanta sai dai har yanzu shigar Sudais shi ne *doguwar riga da hirami* Sudais na da shekara ashirin da bakwai mahaifinsa ya sako shi a gaba kan fa sai yayi aure, sai dai abin takaicin shi ne: sudais bashi da wannan lokacin, sannan yana da zabin macen da yake son ta zama abokiyar rayuwarsa, yana son idan zai yi aure ya samu balaraba yar mutunci wace a haduwar farko zata girgiza masa zuciya sannan ta nuna masa tsantsar so har sai ya gamsu ya aureta dan kuwa shi fa ba zai kali yan matan zamanin nan masuhalaya marasa kyau ya furta masu kalmar so ba, koda kuwa yar waye ko yar wace kasa ce bata isa ba! Zuwa wannan lokaci ya kekara masu gini ya hana mahaifansa aikin komai su dawo sun zama iyayen Uban gida, yayarsa Bilkissu ta haifi yaya hudu kuma duka a gidansa suke wajen mahaifiyarsa, sai kakaninsa suma a bangarensu A hankali ya fara suna, a kano sanusanu sunansa ya zagaye gari harma da makota Tashi daya ya biyawa family dinsa haji, wanda a tafiyarsu sai dai su ne suka dawo shi kuwa ya samu wani reshe na kasuwanci wanda ya fara harkar abayoyi da gwal inda rigima ta bale a gida Momy ta samo masa matar aure kuma aba ya samo masa yarinyar abokinsa mai suna Humaira Karshe dai sai kiran kakarsa ne ya same shi ta shaida masa Hankalinsa ya tashi matuka da jin wai iyayensa zasu yi masa aure, bai zaci zasu dawo kan maganar ba sannan abin har yana neman kawo masu rigima a tsakaninsu Bashi da abokin tambaya , hasalima yakanyi shawara da Hafsa ne, aman wannan abin ya girmami tunaninta Cike da rashin kwarin gwuiwa ya nufo gida sai dai abinda yayi tunani dan samun nasarar su bar maganar sai ma kara daukakata da suka yi Aba ya yanke hukunci a matsayinsa na wanda ya haifi Uban masu gida wato *Elhaj Sudais Malale* sunnan da yan kasuwa da shuwagabani ke kisansa da shi cewar sai dai a wanke masa tsula tsulan yan mata biyu Humaira , da Khairat Hakan kuwa aka yi a ranar da zasu tare shi kuwa ya kaura sabon gidansa na gra gidan da ya amsa kira, gidan da ya kashe makudan kudi ya tsara shi a tsare, dukan family dinsu da muhalinsa a wannan gida, sannan bangarensa daki biyu kadai ne sai can gefe sauran dakunnan Bayan haka da sati biyu ya daga da matansa saudiya wanda tunda suka tafi basu dawo ba sai shi ne ke zuwa yayi wata a gida ko satitika ya juya aman a yanzu kuma abinda iyayensa ke so shine ya dawo gida nigeria dan kuwa ba son zamansa a kasar ta dindindin..... WANNAN KENNAN..... . ......... *CI GABAN LABARI*................. Ajiyar zuciya hafsat ta sauke tana kallon kakarta ta ce" ina alfahari da Yayana Ramatu kakar su ta ce" ba ke kadai ba mu kanmu muna takama da UBAN MASU GIDA! Daidai wannan lokacin mahaifiyar su Aisha ta kawo masu karshen labarin waye sudais a yanda ta karanta jaridar rayuwarsa da kuma yanda take jin sunnansa a kullun a gidan redio.... Cike da bege aisha ke saurare inda Rauda ta ji wani hawaye mai dumi ya biyo gefen fuskarta Bayan kwana uku Mamaki ne ya cika masa kwakwalwa, a sunayen da Hafsa ta bashi ba wanda bai dora a page din Facebook du ya ga sauran aman banda wa.innan yan mata biyu, wai da gaske ne bata da waya kamar yanda Hafsat ta fada? Aman a wannan zamanin daman akoy yan mata haka???? A hankali ya jinginar da bayansa jikin kujera yana kallon kiran khairat na shigowa a iphone dinsa aman ya kasa dagawa, a fili ya furta" who are you? Mai yake shirin faruwa da ni ne na damu da sanin wacece ke haka??????? Lumshe idannuwansa yayi yana mai jin yanda kansa ke sarawa, ko daya baya son damuwa ko wace iri ce hakan na saurin hadasa masa ciwon kai........ To fa me ke faruwa ne??? *❣IDAN KA RAINA INDA KAKE❣* 7⃣ Na: *SAJIDA* Hotuna ne masu yawa a gabansa, wasun su biyun ne wasu kuwa ita daya, a hankali ya dauko wanda take ita dayan inda ta je gidan redio neman aiki wanda du wanda ta je shi yake kira ya hana a dauketa ba dan takardunda basu yi kyau ba sai dan kawai baya fatan ta je tana aiki a gidan redio ko wani gaula yana jin muryarta, shi kansa yana mamakin irin yanda yake kishinta , sai abin haushin na gaba ya ajiye mata envelope a table dinta na aji, ya ajiye mata a cikin adaidaita ya ajiye mata a zauren gidansu aman gaba daya sai ta dauka ta karanta da kyau ta fahimci mai ake nufi sakonta an rubuta mata sadaka aman sai ta rufe ta ajiye a nan inda ta gani, shi ya rasa ta ina zai bilo mata A hankali ya dago wani hoton wanda ya saka gabansa faduwa, da sauri ya kalo saurayin da ya ba kongilar bibiyarta du inda take ransa a bace ya ce" ban yi maka gargadi da irin wannan hoton ba?? Da sauri saurayin ya tsurawa hoton ido kadan, shi dai bai ga ba inda hoton ya nuna abubuwan da ya hana, aman kuma ogansa yake fada haka Ka daina kureta da kallo Samir! Ka gane na fa saka aikin nan ne dan na yarda da kai, karka yarda ka bani kunya a lamuran *Mata* domin idan har wani abin batanci ya bilo a tsakanin abinda na saka ka a dalilin *Mata* ina gudun aikata abinda za.a ji kunya! Ya zaka dauki hotonta gaban gashinta a fili, oya ka bani cameran da ka dauka idan ka fita ka sayi wata sannan ka kiyaye gaba wannan shine kuskure na farko kuma na karshe Ajiyar zuciya Samir ya sauke gannin ba wani baban laifi bane ya aikata, aman duda haka ya shiga baiwa ogansa hakuri sosai sannan ya mika masa yar karamar camerar da ogan nasa ya bashi daman dan dauko masa yarinyar da ya lakaba mata sunnan *MATA* Haka ya fito ya bar ogansa na tunanin hanyar da zai bi dan gannin ya kilaceta wa garwaya da maza ko fitar da muryarta har wani saunan ya ji..., Samir na fitowa ya shiga sauri dan zuwa siyan wani cameran kafin gobe dan kuwa ya tabata a gobe ma sai ta fito dan neman aikin shi kam ya rasa ta ina zai bilo ya hana wannan aikin shi kam yana cikin tsaka mai wuya domin aiki ne mai hatsari sannan mai romo Zaune take saman tabarma tayi dare dare ta saka mahaifinta a gaba, gefenta aisha ce itama da takardu a envelope sun yi shiru gaba dayansu can mahaifinsu ya nisa ya ce" aa, abin da mamaki domin na kaiwa wannan yaron takardunku salihu takardun nan ya duba ya tabatar min lale takardun sun yi kyau kuna iya samun aiki da su a fannin kasuwanci ko gidan jarida kai harta asibiti gefen ciren takarda sai dai abin mamaki har yanzu an kasa samu koda an dauke ku sai a yi kiranku a baku hakuri ni na rasa inda zan kamo Ajiyar zuciya Rauda ta sauke ta ce" Aba, ni kaina abin nan na daure min kai, harfa wannan asibitin karami na je na kai takardar nan aman ba.a dauke ni ba ranar Aunty Aisha ta hada ta kai gidan sauki inda ake kasuwanci turawa ne a wajen aman har yanzu shiru ba.a kiraye mu ba, gashi lokaci na kure mana wannan shekarar dole sai da isasun kudi Aba Ta karashe murya a raunane Aisha ta dago idannuwanta jajir ta ci kukan takaici ta ce" Aba, dan Allah ka janye rantsuwar nan Mama ta je wajen yar uwar nata ta karbo mana koda rance ne mu je mu zuba Aba idan bamu samu manyan takardu a karatun nan ba wani daukaka zamu samu ba , aman wannan takardar zata bamu damar samun aiki mai tsoka Sai da ta kai aya Malan Ahmad ya sauke ajiyar zuciya, irin abinnan na damunsa sosai fa har cikin zuciyarsa, wani lokacin har hakan na saka shi tambayar kansa shin yayiwa kansa da iyalinsa adalci kuwa da ya ki karbar tayin aikin da aka masa ya dawo ya bar iyalansa a cikin kunci da talauci? Sai dai wani sashi na zuciyarsa ya sanyaya da ya tuna sabawa Allah ya ki yi, dan haka kasancewarsa a haka Haka Allah ya so ya ganshi, shi bai isa ya canza ba shi kuwa ba zai canza hanya dan kawai ya faranta ran Aisha da Mahaifiyarsu ba, to aman idan basu samu aikin nan sun yi ba sai dai shekarar ta tafi haka? Ba tare da ya kula maganar Aisha ba ya maida hankalinsa kansu ya ce" ba zaku yi kunya a rayuwa ba, ku dai ku ci gaba da adu.a , wani jinkirin alkhairi ne Allah ya kawo maku mazaje na gari hakan shine baban burina domin kuwa shine baban jin dadi da zaku samu duniya da kiyama Mikewa Aisha ta yi ta fada daki mahaifiyarta na sauraron radio ta je ta konta saman tabarmar leda ta yi lamo ta afka tunanin mutumin da ya zamo mata jiki, a hankali ta lumshe idannuwanta ta furta" idan iyayena ba komai bane basu da komai .... ni zan nemi kudi ko ta halin yaya sannan zaka aure ni *SUDAIS* domin ni ban hango namijin da ya dace da ni na dace da shi sama da kai, sannan da yardar Allah idab na hadu da kai koda a duban jama.a ne sai na furta maka kalmar so Wasa wasa yau har sauran wata uku a rufe daukan daliban da zasu karanci kasuwanci na shekara biyu kawai wanda da wannan takarda kana da damar shiga ko wani kanfani koda a turai ne ka samu aiki mai tsoka sai dai kudin wannan makaranta masu yawa ne duda promotion ake kafin na yan watannnin nan dan a baiwa yayan talakawa damar samun wannan ci gaba wanda mafi yawancin daliban jami.ar sun fatsama nema dan su samu da yawa sun sami aiki sun fara zubawa yayan masu hannu da shuni har an biya masu wasun kuwa suna cikin paputuka dan gannin sun sami wannan dama Zaune suke a anfani tun karfe bakwai na safe, sai karfe tara managern ya zo wanda bayan ya shiga suka ci gaba da zaman dan an yi masu iso an ce su dakata zai yi masu magana Suna nan zaune wani saurayi mai kalar hutu ya zo ya shige cikin office din managern da ido suka raka shi kafin su kuma juyowa su yo zuru suna jira Da shigar samir wannan office ya zauna yayi introduce dun kansa wa manager sannan ya gabatar masa da dalilin zuwansa wato *ELHAJ SUDAI MALALE* ke son magana da shi Cike da mamaki da farin ciki manager ya karbi waya bayan Samir ya hada su ya yi salama wa SUDAIS Kana ji Elhaj tanko Bashir, Akoy wasu yan mata biyu da suka zo neman aiki , ina so kar ka basu aiki idan da hali ka tura secreriarka ta salamesu ba sai ka gansu ba Cike da mamaki manager ya ce" eh wa.inda suke zaune ba? Ai na ga takardunsu Elhaj sun yi kyau kuma fa Kansa ya dafe yana saman katon bed dinsa dake saudiya ya mike zaune ya ce " ba dan takardunsu basu yi kyau ba, sai dan hakan shi ne bukatana sannan Samir zai baka tajardar kongilar idan na shigo kasar zamu hadu mu dandance maganar Ai manager bai tsaya jin karshen maganar ba cike da farin ciki ya amsa da " tototo an gama yalabe, domin kuwa wannan kongila ya jima yana son ya samu a kala za.a kai shekara biyu sai yau Allah ya yi, Yana mikawa samir wayar ya kirayi secretariarsa ya shaida mata ta salami yan matan nan ba zai dauke su ba ta basu takardunsu Fitowa ta yi suna zaune zaman jira sai gani suka yi an miko masu takardu cewar su je ba zasu samu aiki a nan ba Cike da takaicin zaman da suka yi, kudin motar da suka yi talbace talbace, karin da basu yi ba, sannan ga shi ba samun nasara aisha ta fashe da kuka ta zubar da takardun a gabanta ta dora hannayenta a kai tana kallon Rauda da ta hade rai fuskarta ke nuna abinda zuciyarta ke ciki Tana hawayen ta ce" wai wani irin bakin abu ne ke bin mu haka? Rauda ta kawar da kanta ta ce" kar ki butulcewa Allah Aisha, ba wani abin kawai mu kara hakuri zamu samu ai da saura Cike da Haushi Aisha ta dan daga murya wanda hakan ya sa Samir ya kara daukowa mai gidansa maganar da suke fadi ta ce" haka fa zaki ce, ta ya zaki ce wani ba wani abin, ke idan ke bakya ganni ni ina ganni, yaushe zaki ce wani ma samu bayan yau sauran wata uku? Idan muka kara wani watan kin tabata zamu samu aikin da zai ishe mu biyan makarantar??? Rauda ta ce" to idan bamu samu ba ba sai mu yi hakuri ba? Aisha cike da jin haushi ta ce" walahi a bakinki, karya kike , walahi ba zan hakura ba, haba baki da hankali ne? Abinda zai saka na kara samun kusanci da shi kike yi min bakin ciki? To walahi sai na samu kuma sai na yi dan kuwa a yanda nake sonsa ke ko sata sai na yi dan ba zan iya hakura da shi ba Wannan karin ranta itama ya baci cike da jin haushi ta ce" to ai sai ki kwata aunty Aisha haba, kan wannan banzan dalilin naki da wuya mu samu biyan bukata , ni ina neman takardar nan ne dan na samu ci gaban da zan karawa mahaifana farin cikin rayuwa ba wai wani abin ba, aman ba komai Allah yayi mana zabin da ya fi zama alkhairi aman ki sani wannan mutumin da ya saka kika kara rikicewa *na tsane shi na tsane shi*! Dau Aisha ta dauke Rauda da mari a wannan waje wanda har jama.a sun fara tsayawa suna kallon fadan nasu dan kuwa Aisha tana daga muryarta ne, cike da masifa ta nunota da yatsa ta ce" za ki saka na yi maki abinda ban taba tunanin zan yi maki a duniya ba, domin kuwa ina son mai sonsa sannan du wanda ya nuna masa kiyaya ko wanene nima ina kinsa! A hankali rauda ta juya ta fice a wajen wanda aisha ta tatara takardunsu ta bi bayanta itama cike da fushi Da sauri ya katse vidio call din da Samir yayi masa ya zauna ya dafe kansa ya da hannu bibiyu ya afka tunanin me ke faruwa haka? Menene kuna wannan? Yana tsaka da tunanin ya ji danshi danshin ruwa, a hankali ta shiga shafa masa kirjinsa tana kara hade jikinta da nasa, ta mika hannunta ta janye hiramin dake kansa ta cusa hannunta cikin gashin kansa tana sosa masa a hankali sannan tana kokarin hade bakinta da nasa Jajayen idannuwansa ya dago ya zuba su a fuskar Humaira, ba zai iya ba , a yanda yake jin zuciyarsa ba zai iya sex a wannan yannayin ba duda abinda ya tisoshi gaba kennan aman gannin ran *MATA* a bace shima ya hadasa masa da bacin ran mai tsanani Cike da rashin kuzari ya saka hannunsa ya dakatar da Humaira ya dorata saman cinyarsa yana dan jan mata yar yololuwar rigar da ta saka Hannunsa ya mika ya dauki wayarsa bai sauketa a samansa ba ya latso number Mai gidan radio Anfani, yana dagawa ya fada masa bukatarsa ya kashe sannan ya zubawa Humaira idannuwansa, Humaira yarinya ce yar gayu, farinta har ya zarce na *Mata* , ta hadu karshen haduwa domin ko yannayin halitun jikinta ba laifi Daidai gwargwado humaira na da biyaya duda ana fadin in dai namiji na da kudi kuma yana saki to fa ya zarce wulakancin mace dan kuwa Humaira dalilin aurenta da Sudais ba ita ba yan gidansu kansu sun huta A hankali ya shafa gashin kanta ya lumshe mata ido bai iya furta mata komai ba ya mike ya fada wanka dan samun yar nutsuwar da zai iya zuwa shago ya fitar da kayan da zai tura Nigeria Yana tsaka da saka kayansa yayi tsam ya zurawa girar idannuwansa ido, a hankali ya furta" Mata, ban so dawowa nigeria nan kusa ba aman bani da zabin da ya huce na zo dan na ga alamar kin rantse sai kin yiwa wani aiki ...... Farin ciki na neman kauracewa yan matan nan biyu da mahaifansu dan kuwa damuwar Aisha ta tsananta wanda take jin haushin kanwarta dan ta nuna ta daina zurfafa soyaya da kiyaya dan ba kyau hakan ya saka bata sakewa kowa tana fushi da kowa, hakan ya shafi walwalar iyayen Zaune take tana kada miyar yauki, gefenta radionta ne tana sauraron shirin mu tatauna, ana tsaka da shirin aka dakatar dan gabatar da sanarwa mai mahinmanci wanda Farida Alkali ke gabatar da Cike da zazakar muryarta ta fara sanarwar kamar haka" *KANFANIN ABAYA AND GOLD* na *ELHAJ SUDAIS MALALE* suna bada sanarwar neman ma.aikata masu takardun shedar sun karanci kasuwanci daga ranar litinin zuwa asabar za.a rufe dauka bisa albashi naira dubu dari hudu du wata! Allah ya baiwa mai rabo sa.a Butar dake hannunta ta saki cike da murna, da sauri ta karaso wajen mahaifiyarsu ta ce" mama, kina ji kuwa? Kanfanin Sudais ne Cike da tausayawa mahaifiyarta ke kallonta ta ce ".... *❣IDAN KA RAINA INDA KAKE❣* 8⃣ Na: *SAJIDA* Cike da tausayawa mahaifiyarta ke kalonta, dan kuwa ta fahimci halin da yar tata ke ciki sai adu.a dan a ina zata samu abinda take so? Aishanta mai gayu da kyau du ta rame dalilin tunani da ta sakawa zuciyarta na mutumin da yayi mata zara ta ce" eh kina ji ma.aika zai dauka aman ai ku takardunku basunkai inda ake bukata ba ko? Rauda dake wanke tufafinta ta ce" mama, ai basu fadi girman takarda ba , ko zuwa muke mai yiwuwa mu dace Da sauri Aishar dake fushi da Ita ta ce" yawa sister, kin ga gama wankin mu je mu canzo envelop mu fara shiri tun yau idan Aba ya zo ya tofe mana su da adu.a ko Allah ya sa mu dace Murmushi ta yi har cikin zuciyarta tana son gannin hakoran yayarta tana farin ciki, a ranta ta yi adu.a cewa" Ya Allah wannan soyaya da yar uwata ke yiwa wannan bawa naka kar ka jarabeta da shi, ya Allah idan har mutumin arziki ne mutumin mutunci ne ka karkato da tunaninsa wajen yar uwata ka sa ya ganta da kansa ya sota ya aureta, idan kuwa ba malamuncinta bane Allah ka cire mata wannan zazafar soyaya ka saka mata ta malamuncinta ya ubangiji Hakan kuwa aka yi, sun yi shiga na mutunci atampa da hijabi har kasa mai hannu , suka shiga adaidaita , idan ka kali fuskokinsu zaka karanci abu biyu ne, Rauda fuskarta na nuna tsantsar zulumi ita kuwa Aisha tsantsar fsrin ciki A gaskiya Rauda ta sare, hankalinta ya tashi irin yanda ta hango tsaruwar ginnin wannan Kanfani, ko ina camera ne da jami.an tsaro, sannan yan mata tsala tsala sun bayana da samari kowa da takarda a hannunsa na neman aikin nan, Da wuya ka ga wani a wajen napep ta sauke du yawanci da motocinsu, wasu da mashin dadaya ne Ake ajiyewa a juya mutanen fa da dan yawansu Da sauri Aisha ta damki hannunta suka zo shiga suka mikawa masu tsaron kofar envelop dinsu sai dai abinda ya basu mamaki mata ne suka duba takardun suka basu suka shige Tafe suke suna bin hanyar da aka rubuta nan ne wajen daukan ma.aikatan har suka karaso kofar wani gun da suka ga mutane a zazaune layi ne dan haka suma suka bi layin Sun dan jima a zaune, kusa da wani namiji suke zaune ya ishe su da yawan magana sai ga wata mata ta fito da irin kayan securitie a jikinta ta nufo wajensu Abin mamaki tana karasowa ta yi nuni da su Rauda ta ce" ku mu je ko? Kallonta suka yi kafin suke kallon juna, da mamaki suka kuma kallonta da idannuwanta ta yi masu signa kafin ta juya Da sauri aisha ta damko hannun rauda suka mike suka nufi kofar Kafin ka shiga sai an caje ka da irin abin nan na caje mutane sai dai abin mamaki waje kawai mutumin ya basu ko kalonsu bai ba suka shige Gabansu ne ya yanke ya fadi sakamakon gannin tsaruwar wannan waje, cike da tsoro Rauda ta damke hannun Aisha ta fara kokarin janta da su koma domin har ga Allah ita fa ta tsorata da irin dukiyar wajen nan, haba dole a saka tsaro irin haka dan kuwa abin ba na wasa bane Tirjewa Aisha ta yi ta ki bata goyon bayan su juyan, a hankali ta ce" Rauda ki natsu mana kina ganni mu suke kallo Dago da idannuwanta ta yi, hakan ne kuwa su suke kallo! Mata ne guda uku .. ba bahausa a ciki, larabawa biyu da baturiya guda A hankali suka karasa suka mika takardun su wa macen ta farko Buda takardun ta yi, cike da mamaki ta dago tana kalon su, abin nan na bata mamaki, to aman wa.innan yan matan mai din oga ne da ya umarci a dauke su aiki ko tambaya kar a yi masu? Angelina da take matsayin mai kula da bangaren gold tana kara tace karkonsu ta kali Basma cikin yaren turanci ta ce" aman suna da kyau yan matan nan, daman a nan kano ma akoy yan mata masu kyau haka? Kafin ta bata amsa dan ecouteur din dake kunnayensu a markaye wanda aka hada su magana da Sudais ya dauki amon muryarsa cikin wannan maganar nasa marar taushi ya ce" ba abinda na saka ku kennan ba, na saka ku ne ku dauke su ba tare da kun yi masu wani dogon magana ba dan haka ita ramaman nan sosai ku saka ta a matsayin mai kula da harkar takardu ta kawo office dina, ita kuwa dayar ku kaita wajen su Basma Yana kai aya yayi shiru ransa na tafarfasa ya ji haushin angelina, shi fa a gaskiya idan ya ga abin nasu hauka ne kan *MATA* sai ya dakatar da su aikin nan baya ce masa komai ya kawo gaba daya mata musulmai sannan ya saka tsaro a cikin sun ma domin yanzu duniya ta ki gaskiya mata kansu neman mata suke Cikin gagawa aka bi umarninsa aka tafi da su kowace aka nuna mata wajen da zatana aiki sannan aka fada masu tun gobe zasu fara.... Farin cikin da suka shiga ya hana su tsayuwa mamakin wannan sa.a tasu ta yau harma su dasa ayar tambaya a hakan, aman abinda suka sani shine Allah ne ya tsaya masu ko tambayoyi ba.ai masu ba du kuwa da irin kannantar takardunsu bayan wa.inda ke tare da su du sun fi su da yannayin girman takardu da komai Da matukar farin ciki suka dawo gida, da gudu suka shige suna masu shaidawa mahaifiyarsu cewar an dace Cike da farin ciki ta rungume su tana yiwa Allah godiya, har ta hangota ta warke duda basu sani ba aikin mai jimawa ne ko na dan lokaci, ita kam tana fatan mai jimawar ne Yana ajiye wayar ya kashe computersa, ya jingina da kujerar office dinsa yana sauke ajiyar zuciya, tunani ya afka na irin taurin kan *Mata*, a fili ya Furta" *YA ALLAH KA SA TA FURTAN KALMAR SO , ITA KAM BA ZAN WULAKANTATA BA ZAN KARBI SOYAYARTA DA GAGAWA, ZAN ADANNATA A MUHALIN DA SOYAYAR WATA BATA TABA SHIGA BA, MATA KODA BAKI IYA GIRKI BA NI INA SONKI A HAKA SAI DAI BA ZAN TABA IYA FURTA MAKI BA DOMIN HAKAN BAYA CIKIN TSARIN RAYUWANA* yana gama tunaninsa ya mike ya fito ya shiga acenseur ya sauko kasa , a kafa ya shiga takawa yana mai jinsa cikin nishadi domin ko ba komai ya san ya karakiusanto kansa da *Mata* Yana shiga vila dinsa ya dauki mashin cikin mashinan masu tsaron kofar gidansa ya hau ya karasa domin ko a saudiya ginnin gidan Sudais ba na wassan yaro bane Khairat ce zaune saman kujera irin mai juyawar nan tana shan madara da ta yiwa kauri kitif Salama yayi mata, ta juyo tana amsawa ta saki murmushin da ya saka kumatunta girgiza domin khairat yar lukuta ce sosai, ga zaman guri daya ga cin dadi ga gari mai ni.ima mai tarin albarka hakan ya kara mata gudunmuwa wajen kara busuwa jikinta ya kara yin luwaiwai Yana karasowa ta mike ta karaso wajensa ta rungume shi ta ce" welcom habibi! Murmushi ya saki ya ja hancinta ya ce" Khairat, zabin Mahaifiyata, Allah dayib Itama murmushin ta yi ta bi bayansa suka nufi dakinsa domin yau aikinta ne ta taimaka masa ya shirya suka fito dan cin abincin rana duda har yama ta yi Suna gama cin abinci masu aiki suka kwashe suka shiga kimtsa wahen su kuwa suka koma baban falon gidan suka zauna suka shiga hira Humaira sarkin kishi, kai zuciyarta take nesa duda ita a ganninta ta fi Khairat komai aman tana jin haushi idan ta ga baya banbance tsakaninsu Can cikin hira ya ce" ina son zan shiga nigeria cikin satin nan na gaba, na baku zabi wace take son zuwa gannin gida sai mu tafi domin ina kyautata zaton wannan karon zan dan jima a nigeria Cike da mamaki Humaira ke kallonsa, a saninta Sudais baya son zaman nigeria dan kuwa al.adun mutanen saudiya ta daye zuciyarsa aman abin mamaki a wannan shekarar yana yawan maganar nigeria ko dai kuma hankalinsa ya karkata can ne? Kai aman ita gaskiya ba zata so hakan ba dan kuwa kasar nan ita ce daidai da wajen ta yi rayuwa A hankali ta ce" aa, nigeria da alama ta fara kwato incinta domin tana son dawo da elhajin kasarta cikinta ni ko dai can zamu koma da zama ne Sudais ya dan jima yana auna maganar Humaira, lale gaskiya fa ta fada..., kamar yana kara kaunar kasarsa fiye da da, kalonta yayi ya ce" ai ba abin mamaki bane dan dan kasa ya koma kasarsa, may be daman bai tsaya ya tantance dadin kasar nasa da wata kasar ba Tamkar ba ta bakinsa maganar ta fito ba, inda Ya juya wajen Khairath ya shafa cikinta dake ture tamkar mai ciki ya ce" Khairath, ko dai na yi ajiya a nan ne? Khairath ta dago tana kalonsa sannan ta bi hannunsa sa kalo ta kakalo murmushi domin kuwa ita kanta tana kokonton ko ciki ne da ita dan kuwa ta cika kwadayi kwanakin nan sannan bata ga period dinta ba Cike da nuna farin ciki ta ce" ya Allah amen ya rab Da sauri Humaira ta kaleta, bata san lokacin da ta mike ba ta yi bangarenta kar zuciyarta ta buga (Wannaan kennan) Konci tashi yau har satin su Rauda bibiyu da fara aiki a karkashin kampanin Abaya and Gold na Haj Sudais, Yau ya kama litinin kamar kulun sun shirya da wuri, yau koko kawai suka samu da mama ta karbo a gidan lami bata riga ta fara tuyar kosan ba Da gagawa suka tari bos domin kudin wajensu ba zai ishe su zuwa a napep ba Suna zuwa wajen magama hudu bos ta sauke su suka taka a kafa har wajen aikinsu suna tafe suna dan zantawa Wannan kalon kan nasa ya fi a kirga da ya yi, domin kuwa jalabiyar da ya saka bugagiyar jalabiya ce mai shegen tsada ruwan fara kar, ya daura agogo ruwan ash color yA saka safa ash color ya saka takalminsa sau ciki A hankali ya saka dan macaji ya gyara kansa ya nadidiye shi ya dauko hiraminsa ya dora shi Yana gamawa balarabe sak ya bayana a gaban mirrow din, a hankali ya lumshe idannuwansa yana mai rokon allah allah ya sa yana haduwa da *MATA* komai ya zo masa da sauki dan kuwa a irin yanda yake jinta a zuciyarsa kamar ya cire ya huta, daman haka soyayar yake? To fa wacece *MAYAR* NAN? Yanda yake hasashe zai samu ne? *❣IDAN KA RAINA INDA KAKE❣* 9⃣ Na: *SAJIDA* Murmushi ya kuma saki ya fito ya zauna ya rubutawa matansa chek, domin kowace ta roki arzikin zuwa ta ga iyayenta ba zai hana su ba domin shi mutun ne mai adalci Yana gamawa ya fito kamar yanda ya saba ya shishiga ya gaisar da iyayensa da kakaninsa su hafsa kuwa har sun tafi makaranta dan haka ya zo wajen motocinsa ya shiga suka daga Tun daga bakin kofa ya ga yanda du suke ta kazar kazar kowa yana aikinsa ba sanya domin kuwa oga na gari shi kuwa baya son wasa A hankali ya bude motarsa ya fito daga motar ya tsaya yana kallon yanda ma.aikatansa suke gaishe shi ya shiga daga masu hannu dan kuwa idan ya ce amsawa zai yi to fa har yayi.ciwon baki Cike da iza yake takawa yana kutsawa har ya zo bakin koridor din da zai sada shi da office dinsa Kamar ba sadauki ba ya ji gabansa ya yanke ya fadi, ajiyar zuciya ya saki dan kuwa ya tabata hakan baya rasa nasaba da dan zai hadu da *MATA* ne Kofar office din su Basma ya kafawa ido, wato wajen da suke zama wajen da nan suke wuni idan mai son harhar gold ya zo su tafi su nuna masa ya zabi wanda yake so A hankali ya nufi kofar, du takunsa daya sai gabansa ya fadi dan bai san ko tana wajen ko bata nan ba, Har ya dora hannunsa a kan kofar ya ja ya tsaya, ya jinginar da kansa a jikin kofar yana sauraron yanda zuciyarsa ke bugawa tamkar ta dira ta fito daga kirjinsa, a hankali ya furta" ya Allah, mai ke shirin faruwa da ni ne? Mai ke damuna ne? Menene hakan ne? Wai zan shiga wajen nan ne dan na ga MACE , macen da bata san me nake ciki ba, yarinyar da nake matsayin uban gidanta a wannan waje, yarinyar da na tabata na girmeta nesa ba kusa ba, na ce mata me? Ni ba taba shiga na yi wajen nan ba idan suka ganni a yanzu ai dole su yiwa kansu tambaya, ya Allah, du na zama wani kala dalilin wannan damuwa tawa🤦🏻‍♂ Da sauri ya sauke hannunsa, ya juyo ya ga guard dinsa na tsaye inda ya barshi da wayoyinsa Juyawa yayi ya nufi bangaren office dinsa yana mai jin kasala na kara rufe masa ilahirin jikinsa Yana zuwa guard dinsa ya bude masa kofar glass din dake ta walwali ta sha guga , Ajiyar zuciya ya sauke ya lumshe idannuwansa yayi adu.arsa kamar yanda ya saba kafin ya saka kafarsa waje koda dakinsa ne sai yayi adu.a yake shiga Kafarsa na dama ya saka tare da lumshe ido ya bude tar a kan dadayku manyan ma.aikatansa da du suka juyo suna kalonsa kafin suke fara miko masa gaisuwarsu daya bayan daya yana amsawa hankalinsa konce domin kuwa manyan mutane ne , manyan ma.aikata ne na kasa daban daban da na nigeria du wanda ke wajen nan gagarumin mai ilimi ne dan gayu na bugawa a jarida Coridor din da zai sada shi da ainahin offishin nasa ya nufa wanda a cikin coridor din office din Aisha da na wani mai suna Abdul majid wanda ke kula da computer wajen Tunda ya tunkaro wajen yake jin dariya kasa kasa wace ta saka shi daskarewa waje guda, da kyar ya ja numfashinsa ya sauke ajiyar zuciya a zuciyarsa yake fadin ke baki isa ba haba, ta ya ke macen ki ringa saka ni faduwar gaba bayan nine namijin ni ya dace na ringa saka ki jin hakan *MATA* , Cijewa yayi ya gyara tsayuwarsa ya doshi office dinsa kai tsaye sai dai me yana karasowa suna fitowa Ja yayi ya tsaya ya shiga yiwa zuciyarsa fada cewa" ki nutsu ki kama kanki, kar ki manta sai mata ta fara furta maki kalmar so kafin ki karbeta, karki manta ke din ta daban ce, ke din ba zaki iya tunkarar wa.innan yan matan zamanin masu halayar rashin kamun kai ki furta masu kalmar so ba dan kwatakwata hakan bai dace da ke ba, ki nutsu fa! Duda yanda yake gayato jarumta ji yayi yana neman gazawa, lumfashinsa na neman gagararsa A hankali ya kai hannunsa na dama ya bale boturan da ya saka na wuyansa wanda yake ji kamar ya shake masa wuya a yanzu ya saka hannun yana dan shafa wuyan nasa Da sauri guard din nasa ya matso cikin harshen turanci ya ce" sir lafiya? ? Yana kokarin yin magana suka juyo wajensa a tare Aisha cike da mamaki da farin ciki take kalonsa da wani irin yannayi mai wuyar fasara, Alkawarin da ta yiwa kanta, abinda ta jima tana jira kennan, wannan rana ta jima tana tsara yanda take so ta zo mata sannan irin abinda zata yi a ranar Sakin hannun Rauda ta yi wace itama ta yi mutuwar tsaye da gannin ogansu mutumin da ya haukata zuciyar yayarta tsaye a gabansu tamkar a naso shi Aisha ta daga kafarta tana nufar Sudais, wanda hakan ya hadasa masu faduwar gaba gaba dayansu, Shi yana mai faduwar gaban ganninsu gashi ga su a karo na uku, Aisha na faduwar gaban abinda ta yi niyar zuwa ta sanar masa wanda ke hanata baci da sukuni, Rauda na faduwar gaban abinda Aisha zata aikata dan karfin hali wa mutumin da ya fi karfinsu wanda hakan na iya sakawa ta jaza masu hasarar aikinsu (idan abin ya tsaya iya aikin ma ai da kyau) Ja ta yi ta tsaya a gabansa, ta kafeshi da wa.innan idannuwan na mahaifiyarsu masu fizga dan tsananin tsarinsu da girmansu da kyansu, ittafa a yau a yanzu ba sai an jima ba zata amayar masa da sirin dake ranta koda kuwa zai raba gangar jikinta da numfashinta ne Cikin siriryar muryarta ta ce" welcom *SUDAIS*! Gabansa ne ya yanke ya fadi da gannin abinda ke shirin faruwa, bai kai karshen tunaninsa ba ta ce" Sudais, *My Sudais* sunana *AISHA AHMAD* ina tsananin farin cikin dawowarka a wannan lokacin, Sudais ba zan iya ci gaba da rike damuwana ba, Tayi tsai tana sauke ajiyar zuciya ta ci gaba cikin sasarfa ta ce" koda gizo ne kake yi min ba kai bane zan fadawa fatalwanka, Sudais Ka tambayi Rauda, kanwana ce bana iya baci, bana cin abinci bani da sukuni SuDais Ta kuma kiran sunansa wannan karon cikin sanyin jiki ta ce" *Sudais* wanda yayi daidai da jin bugun zuciyarsa na karuwa Da sauri ya dago jajayen idannuwansa ya sauke su a fuskarta, ji yake tamkar ya tsayar da ita , ji yake kamar yayi da baya da baya ya koma ya kasance bai bayana a wannan waje a wannan lokaci sannan a gaban *MATA* ba Katse masa tunaninsa ta yi, ta katse masa lumfashinsa na wucin gadi sanadiyar maganar da ta furta, cike da tabacin abinda take ambata ta ce" *SUDAIS I LOVE U SUDAIS* ka so ni koda bai kai rabin rabin son da nake maka ba, ta hade hannayenta tana kokarin ci gaba da magana Cike da tashin hankali SuDais ya dora hannayensa biyu a kansa, ji yayi wata irin juwa na neman yarda shi, Taga taga ya yi ya kusan zubewa da sauri guard dinsa yayi kokarin tare shi yana ambatar subahannalah sai dai Sudais ya daga masa hannu ya dafe bango da hannunsa na hagu Ji yayi ba zai iya furtawa Aisha komai ba, a daidai wannan lokacin bukatarsa shine ya gansa a gida ya kauracewa kowa da komai ya samu yayi tunani, Saurin juyawa yayi yana kokarin komawa hanyar da ya fito sai dai kafin ya tabuka wani abin Aisha ta rike masa gefen jalabiyarsa, muryarta na rawa ta ci gaba da magiya kan ya saurareta kar ya tafi ya barta a wannan halin da take ciki dan bata san irin abinda zao iya samunta ba😭 Cikin zafin nama ya juyo ya janye hannunsa kafin ta tantance wani abin ya dauketa da gigitacen marin da ya saka Rauda da Guard dinsa mugun zabura Cike da tashin hankalo Rauda ta tako da gudugudu ta tare Aisha ta fado jikinta ta riketa sosai sosai , Da wani mugun kallon tsana ta dago ta sauke idannuwanta kan fuskarsa wanda ya kusan saka zuciyarsa bugawa dan kuwa da wannan kallon da ta yi masa sai ya gwamace dama mari ta wanka masa Aisha ta cukuikuye hijabin Rauda ta riko hannun Rauda jikinta na mugun bari, hankalinta a tashe, Har wata kwallah ce ta tarunma Rauda a idannuwanta, a hankali ta rikw hannun yayar tata murya kasa kasa ta ce" mai ya kai ki kallon wannan mutumin da baya gannin mutuncin wanda ya rabe shi furta masa irin wannan kalma? Aunty ki yi hakuri da wannan soyaya domin bata da anfani Aisha ta ce" Rauda aa, Rauda ki yi shiru Shirun kuwa ta yi ta samu da kyar ta kama Aishar suka mike ta kamo hannunta da niyar ratsa ta gefensa su yi tafiyarsu Idannuwansa ya zaro, domin gaban goshinta gashinta ya fito sosai sanadiyar cukuikuyeta da Aisha ta yi, A shigowarsa kuwa ya tarar da maza sosai , ba tare da wani dogon tunani ba ya yi gaba da sauri ya fice su yayi waje Harara rauda ta raka shi da shi sannan ta tsaya tana kara baiwa yar uwarta hakuri Suna cikin haka Basma ta shigo wajensu , sai ta nuna bata ma san abinda ya faru ba ta ja su cikin office din Aishar, nan ta jawa Rauda hijabinta ya rufe mata gaban goshinta da kyau suka zauna suna tataunawa inda wayarta ta yi ta ringin sai mikewa ta yi ta kara ba tare da ta yi magana ba Muryarsa a dagule ya ce" bata fito gashinta a fili ba dai ko? Basma ta amsa sa da " eh na dawo da su office gaba dayansu na rufe masu kansu Ajiyar zuciya ya sauke ya datse kiran ya kurawa hanya ido inda direba ya sake baiwa motar wuta A hankali ya ce" Ya Rab, ba itaba, Allahna ba itaba, *MATA* dan me kina tsaye kina kalo hakan ya faru? Mai ya sa baki hana faruwan hakan ba, Idannuwansa yayi gagawar rufewa dan a lokacin hararar tsanar da ta jefo masa ta kuma fado masa a idannuwansa , da sauri ya dafe kansa yana ta maimaita innalilahi wa.ina ilaihi raj.une....................... Comment ko?🤧 *❣IDAN KA RAINA INDA KAKE❣* 1⃣0⃣ Na: *SAJIDA* Haba sis ba zan dawo ba, ba zan dawo ba aikin nan mun bar shi daga yau ! Rauda ke fada cike da bacin rai da kunyar abinda yar uwarta ta aikata yanzun Rauda Ta ci gaba da fadin" a matsayinki na mace aunty, mace da aka sani da kunya da jan aji, mace da aka sani da tarbiya da wayo da dabara, haka kawai ki tarbi gaban wannan garjejen katon ki furta masa kalmar so? Aunty ko mazan a yanzu sun daina irin yanda kika yi, su kan yi dabara ne su jewa mutun ta inda zasu samu gamsashiyar amsa ba wai kawai daga shigowarsa ki tare shi ki furta masa kalamai haka sannan ki yi tunanin zai saurareki, kin ga mu yi tafiyarmu sannan mu yi hakuri da aikin da karatunma gaba daya aunty dan kuwa koda bamu yi tafiyarmu ba shi zai kore mu ne! Da mamakinta Aisha sai ta saki murmushi harda dan sautin dariyarta mai kayatarwa ta ce" lallana, menene? Wannan abin ne ya daga maki hankali kike kai kawo har kike ikirarin mu bar aiki? Idan muka bar aiki ya zamu yi da cikar burikanmu? A ina zaki samo kudin karatun da kike mafarkin yi dan ki talafawa DAD? Ta dan tsagaita sannan ta dafe daidai zuciyarta ta ce" ni kuwa ta ina nawa mafarkin zai cika na samun muradin zuciyata? Wannan ai ba komai bane lallana, wannan abin da kika gani somin tabi ne, wannan marin da yayi min sister ai farkon sanina ne, sau nawa kika ga an yi haka an ci riba? Na tabata zai bani hakurin marin nan da yayi min Cike da mamaki baki bude Rauda ke kallonta, can ta ce" kina nufin Aikin nan da muke kina yinsa ne dan ki sami wannan mutumin? Aisha ta yi murmushi ta ce" burina kennan, ina da burin na sami matsayin da koda bai so ni dan kyauna ba, bai so ni dan Halayana ba, bai so ni domin Allah ba, zai so ni dan arzikin da zan yi , sai Allah ya taimakeni na zo ma.aikatarsa, Lallana duba ki gani wannan daular watarana zan zama matar mai wajen nan? ??? Ta mike tana juyi tana sakin murmushi ta ci gaba da fadin" kin ga zan sayi wuleliyar mota, za.ina daukanki da mama mu zagaya gari, zan je na yiwa su Amina, du sati biyu za.ina leka dubai, zan rushe gidan nan na murje shi , zan sayi vila na zuba talakawa ma.aikata oh sister zan yi rayuwA! Cike da takaici Rauda ta dauki yar pos dinta ta fito bata kuma furtawa Aisha komai ba ta zo wajen kujeru na cafetaria ta zauna ta zuba tagumi ta fada kogin tunani No no no , Ya Allah, ya Rab ka farkar da ni a wannan mafarki mai firgitarwa, Allahna ka farkar da ni a irin wannan mafarki domin sam bai dace da ya faru da ni ba Khairat da ta shigo cike da gajiya ta yi masa salama a gefensa Dago da kansa yayi, idannuwansa da suka kade sukai jajir ya zuba mata yana mai amsa salamarta Karasowa ta yi kusan shi tana cewa" Husband lafiya? Me ke damunka? Ya aka yi ka dawo da wuri haka? Kuma dago da kansa yayi da yake tsananin sara masa, bai iya ce mata komai ba sai mikewa yayi ya cire doguwar rigarsa ya rage masa daga shi sai dogon wandon dake ciki ya karasa wajen da ba moket ya konta kansa na kallon sama jikinsa ma wato konciyar rigingine, ya kai hannayensa wajen kansa ya shiga yin abdomino A kadan ya yi ya kai sau hansin bashi da niyar dakatawa Mikewa ta yi , abinka da mai jiki rigar du ta shige jikinta ta ja ta gyara ta nufi firij, ta dauko ruwa Awa, ta dauko kofi na kwalba ta nufo wajensa tana tunanin abinda ke damunsa? Domin hakan na daga cikin dabi.unsa idan ransa ya baci yakan zo ne yayi ta sport har sai an hana shi ko ya ji ya kasa tashi Tana zuwa a hankali ta zauna a nan kasa, ta jakudo ta daidaici ya dago ta yi gagawar saka cinyoyinta yana dawowa sai kansa ya sauka a saman cinyarta Kokarin kuma mikewa yayi ta yi saurin rike hannayensa, ta dora dayan hannun nata ta cire masa hiramin kansa, ta shiga shafa masa kansa da kirjinsa tana sauko da hannunta har kan fuskarsa tana shafa sajensa da yayi konce lufluf tana kara yi tamkar tana shafa mage A hankali yake kontar da kansa har ya sakar mata nauyin kansa, idannuwansa a lumshe sanu a hankali har lumfashinsa ya fara daidaituwa har ya dan dawo normal aman tana iya hango yanda zuciyarsa ke bugawa Sosai ta yi mamakin abinda ya saka masa damuwa haka, A hankali ta ce" *yayanmu* Bai amsa mata ba aman ta san yana jin ta dan haka ta ci gaba da shafa kirjinsa ta ce" me ke damunka ne *UBAN MASU GIDA?* bai amsa ba dai , itama bata daina shafarsa ba sannan bata maimaita tambayarta ba, A kala ya kai minti goma da ta yi masa tambayar, a hankali ya miko hannunsa na hagu ya riko hannunta na dama hakan ya bata damar bin damtsen hannun da kallo yanda jijiyoyin wajen birde birde da su, makwat ta hadiyi yawun da ya tsaye mata a makoshi tana mai kara hamdallah da Allah ya malaka mata miji irin wannan Tunaninta ya katse daidai lokacin da ya dora hannun nata daidai saitin zuciyarsa, Da sauri ta kai kallonta wajen, tsoro ya kamata, tsoro take kar a je ciwon zuciya ne yake? Sai dai wata zuciyar ta bata amsar da ciwon zuciya ne da ya kasa aiwatar da komai domin kuwa ciwon zuciya ai ya fi karfin tunanin mai tunani Idannuwansa ya bude ya sauke su a fuskarta wanda ya saka gabanta ya kuma yankewa ya fadi sanadiyar jan da sukayi Da kyar ya samu ya ciro magangannun bakinsa ya ce" *KHAIRAT, kadara ce, wace na kasa tantance fara ce ko baka, abinda na sani gwagwarmaya ne mai zafi wanda cin galaba a ciki sai an dage da adu.a da kuma hakuri, Khairat ya akayi hakan ya faru da ni? Mai ke shirin faruwa da ni? A tunanina BAN RAINA INDA NAKE BA! Domin ina baiwa gonakina shuka da wadatacen ruwa daidai gwargwado, sai gashi wata kadara wace Allah kadai ya san me zata zame min gobe tana neman dauken natsuwana, Khairat ki tayani da adu.a abinda nake ciki Allah ya bani mafita domin ni ba kowa bane, a gaban wannan kadara nakan kasance sauna sususu wawa marar tunani marar anfani, bani da zabi, nakan rasa duniya nake ko kiyama, ki tayani da adu.a na fi karfin hakan Khairat* Magangannun mijinta sun saka ta a halin tunani, Khairath ta kasance mai sanyin hali ba kamar Humaira ba, ta kasance mai saukaka abu , hakan ya saka ta sauke ajiyar zuciya domin sai tunaninta ya bata cewar ko kan harkar kasuwancinsa ne? Ta tabata baya son ta zurfafa shi ya saka ya bata abin a dunkule ... hakan ya saka ta jimke hannunsa dake kan kirjinsa da nata hannun ta ce" *bawa baya tsalake kadararsa, du iya dubararka sai ta riskeka, kadara abu ce da Allah yake kadartowa bawansa, kowani bawa da irin jarabawar rayuwarsa, fatanmu Allah subahanahu wata.ala ya bamu ikon cinye jarabawar rayuwarmu, ya kadarta mana farar kadara UBAN MASU GIDA* Bai kuma furta mata komai ba ya lumshe idannuwansa ya shiga adu.ar Allah ya sanyaya masa abinda ke shirin kuno masa koma ya ce ya kunno masa *CIGIYA* *NI SAJIDA YAR MUTAN NIGER INA BADA CIGIYAR LITATAFAINA MASU SUNA DUK KARYAR KADA, BANI DA ZABI, NEMAN NA KAINA, DAGA TAFIYA DAUKAR SOJA, YAR MAHAUKACIYA.....! DOCUMENT COMPLET* DUK WANDA Allah ya sa yana da ya taimaka ya turo min ta wannan number *92466605* *❣IDAN KA RAINA INDA KAKE❣* 1⃣1⃣ Na: *SAJIDA* *Cigiya* *NI SAJIDA YAR MUTAN NIGER INA BADA CIGIYAR LITATAFAINA KAMAR HAKA: YAR MAHAUKACIYA, DUK KARYAR KADA, NEMAN NA KAINA, BANI DA ZABI, DAGA TAFIYA DAUKAR SOJA, DOCUMENT COMPLETE DAN ALLAH WANDA ALLAH YA SA YANA DA SU YA TURO MIN TA WANNAN NUMBER 92466605 NA GODE* Tunda ta zauna a cafetariar nan bata furta kalma daya kwakwara ba, idannuwanta na kallon waje guda tana tunani, abinda yafi tsaye mata a rai shine du wannan wahalar da suke sha daman Aisha dan kawai ta malaki wannan mutumin ne? Daman ba dan su talafawa rayuwar iyayensu bane? To aman Aisha tana da hankali kuwa? Mai ya sa take wasu abubuwan? Yaushe Namiji koda dan gwal ne zai daga hannu ya wanka mata mari aman wai ta furta kalmar cewa wai ai ya lura da ita? Irin yanda maza dai ke bin yan mata har su amince masu da soyaya take son yi? Abin nan yana daga mata hankali, soyayar nan da Aisha ke yiwa wannan bawan Allah tana daga mata hankali domin kuwa irin wannan lamari yana iya kai ta ga halaka! Hajia lafiya kuwa??? SALIF saurayin dake kula da harkar cafetariar wanda du wani abu sai ya biyo ta hannunsa kafin ya je wajen masu girkawa da sauransu , Salif saurayi ne mai ilimi, musulmi ne da ya karanci fanin kicin ya fito chef, Salif yana da mutunci bashi da raina mutun, sannan akoy adini Salif shi ke rike da gidansu, saurayi ne bai taba aure ba Allah ya taimake shi ya samu wannan aiki a wajen Uban masu gida Firgigit ta dawo a duniyar mutane ta yi saurin dan jan kujerarta baya domin sai ta ga kamar ya dan matso kusanta sosai Salif ya ce" sorry, ai mun tsorata ne domin na jima ina magana baki motsa ba Raudat bata iya ce masa komai ba sai ajiyar zuciya da ta sauke ta kawar da kanta Menu na abubuwan da suke da a wajen ya miko mata, kalolin abinci ne wanda a cikinsu lipton kawai ake yi kyauta aman dukan sauran kudade ne domin ko kapicilo sai ka biya dubu guda Sai a wannan lokacin kanshin wajen ya fara buso mata, sai a sannan ta ji wani irin sanyi na ac na ratsa kashi da bargonta, da sauri ta daga kanta wajen jeux de lumiere din dake hasko wajen, nan ta fahimci inda ta sanyo kafa Tunani ta afka, ita dai a jakarta naira dari biyar ce, wace zasu cacafta kudin yau da na gobe ne kowa da nasa a jaka domin idan bus ne baki danja ake ajiye su Dago da kanta ta yi, ta kali ruwan Awa da aka ajiye mata wanda haka ake yi idan dai ka shiga wajen nan to za.a yi maka kyautar ruwa masu sanyin ni.ima Ajiyar zuciya ta sauke ta ce" excuse me plz Ta fada tana mikewa dan barin wajen Murmushi yayi, a yanda ya fahimta tana cikin matsi ne, sai yayi murmushi kawai ya bita da kallo har ta fice haka kawai ya tsinci kansa a cikin nishadi na wannan dan lokacin da ya kali wannan baiwar Allahn Yau tafiyar kowa tasa yayi, tana zuwa gida wanka ta yi domin tana cikin fashin salah, ta zauna ta dauki litafin hausa mai suna *Neman na kaina*, tana jin dadin yanda ta cikin litafin le neman halalinta ba tare da ta kauce hanya ba Raudar na ciki ne? Muryar mamansu ta katse mata karatun ta amsa tana fadin" eh mama gani na zo ne? Shigowa ta yi tana fadin" aa aa, Zama ta yi gefen Rauda ta karbi litafin hannunta ta maida dubanta wajen Rauda wace itama ta tataro hankalinta wajen mahaifiyar nata Nana mariama ta ce" Rauda, wai ya haka nake jin shiru haka? Ita Aisha idan na yi magana sai ta nuna ai ita ga wanda take jira ke kuwa shiru kawai ba magana Rauda ta lumshe idannuwanta bata ce komai ba, mamanta ta ci gaba da fadin" ni na rasa mai ke damunki haka? Mai kika rasa na ya mace aman na kasa samun wanda zai fito yana son ki da aure, ko dai ke kike korar su? Ajiyar zuciya Rauda ta sauke, a hankali ta ce" mama, aman ai ina da manema ko? Nana Mariama ta ce" ke dan Allah kar ki kawo min wannan zancen, su waye maneman naki? Daga mai bayar da hayar kura, sai malamin primari, sai mai kanti? Ke kina tunanin zan amince da wannan shirmen ne? Ko daya wannan ba abin duba bane dan haka ki yi zuciya irin na yar uwarki ki zakulo min wani elhajin nima nan da yan kwanaki na zama uwar hajiyoyi Rauda kasa furta wata kalmar ta yi domin abin ya girmami tunaninta, mahaifiyarta ta mike ta fita, har ta tafi ta dawo ta dage dan labulen kofar dakin nasu ta ce" sai dai kar ku manta daga ke har yayarki abinda bana gajiya da maimaita maku *duk wace ta amince da Da namiji ba da aure ba ban yafe mata ba!* Tana gama fada ta fice Rauda ta yi murmushi mai kuna ta gyara shinfidar katifarta ta konta ta daina karatun novel din domin ta daina jin dadinsa .Washe gari. A makare Rauda ta farka tana mamakin bacin da ta kwasa, tana duba agogo ta ga bakwai da minti ashirin da hudu Cike da mamaki ta kai dubanta wajen Aisha sai dai wayam bata nan, Sai a lokacin hancinta ya jiyo mata kanshin turarenta sannan wajen kayan kwaliyarta ta cakula su Ajiyar zuciya ta kuma saukewa a ranta tace kennan Aunty tafiya ta yi ta bar ni Mikewa ta yi cikin hanzari ta shiga wanka , Tana fitowa ta zauna ta shafa mai ta dan murza farar hoda ta shafa man lebe ta fito tana dan gagawa ta gaisar da iyayenta ta fice a lokacin har takwas sauran kadan Tana fita ta ga Abdurrahman, cike da mamakin ganninsa take gaisar da shi, ta yi mamaki ne domin ita batai masa kwatatancen gidansu ba, Ya sha farin yadinsa, ya kafa hula baka da takalmi baki, ba laifi ya fito domin kuwa sutura ita ce mutun Tana gama gaishe da shi ta mike da niyar tafiya Da sauri ya ce" aa, Rauda sauri kike haka? Rauda ta ce" eh wly ka yi hakuri ina sauri ne na tafi dan kar latin nawa ya yi yawa Da sauri ya hau mashin dinsa da ya sha wanki ya ce" ki yi hakuri na kai ki mana Hajiya Rauda, kin ga a hanya sai mu tatauna domin kuwa na sha wahala sosai kafin na samu na zo wajen nan dan na kai sati uku ina zuwa jami.a da kyar aminiyar Auntynmu(Aisha) ta yi min kwatancen gidan Rauda ta ce" eyah, haka, aman ka yi hakuri Zuwa wani lokacin zamu zauna aman yanzu gagawar dai nake, kuma ka ga ba zan hau mashin dinka haka kawai ana kalona ba Murmushi yayi yana kokarin ci gaba da zubar ta yi gaba abinta Sauri take zubawa cikin doguwar rigarta ja, ta yane kanta da mayafin rigar baki yar pos dinta baka sai takalminta irin takalmin robar nan baki Shar da ita domin sutura komai arharta takan yiwa jikin Rauda kyau ne domin kirarta sai dai a ce masha Allah Mai adaidaita ta kai hudu ta tsayar kowace sai dai ace mata ai ba zasu kaita a dari biyu ba Kara saurin tafiyar nata ta yi ta karaso wajen titi ta tari bus ta shige Abinka da bus sai da aka dauki lokaci kafin ake ajiyeta bakin titi , Tunanin tafiyar ta yi, ta dubi kudin hannunta, Har ta yi niyar yin tafiyarta da kafarta wani abin yace mata kin ga Rauda ki bi aikin nan naki a sanu kar ki bale shi, domin kuwa a jiya kun yi laifi kar ki kara a kan wanda yayarki ta aikata Idannuwanta ta rufe ta tsayar da dan acaba Naira hamsin yace zai kaita dan haka ta haye ya tayar ya kwasheta da mugun gudu Yana zuwa bakin ma.aikatar ya ja ya tsaya Ta je sauka kafarta ta dan gurde hakan ya sa ta yi saurin dafe kafadarsa ta hagu tana ambaton sunnan Allah, Shima yayi tunanin faduwa zata yi dan haka ya dan tarota kadan yana fadin" sanu a hankali dai hajiya kar ki yi ki ji ciwo Kamar daga sama idannuwansa suka sauka a wannan abin, domin tunda ta zo ya zauna gaban cctv ya tsura wa ecran ido yana mamakin yanda aka yi bai gansu ba Yana nan ya ga shigowar daya banda daya Hankalinsa dai bai konta ba yana tsoron kar a je itama aikin ta zo bari dan haka ya hade fuska ya ki bata damar ganninsa ko fita bai yi ba dan kar ta hadu da shi ta gabatar masa da takardar barin aiki Yana zaune ne yana duba time yana kallon wajen zaman kowace, dayar na nan dayar bata zo ba Kamar daga sama idannuwansa suka sauka a kan abinda ya faru Kansa ne ya sara masa nan da nan zufa ta karyo masa mai zafin gaske Ji yayi jikinsa ya fara bari, kwakwalwarsa tamkar ana yakuna masa ita ne Mikewa yayi da wani irin karfi ya cire hiramin kansa yayi wurgi da shi ya fara mutsutsuka ido lumfashinsa ya fara sama yana kasa sakamakon bacin rai da sabon yannayin da yakan tsinci kansa a ciki idan ya shafeta Samir da yayi kira tun fitowarsa ya shaida masa ne ya samu shiga bisa jagorar Aisha da ta yo masa jagora Suna shigowa sukai tozali da Sudais a cikin wannan yannayi A tare suka nufe shi, Samir na salati yana sanar da ubangiji , Aisha kuwa ta fashe ta kuka ta ja ta tsaya jikinta na bari na gannin halin da muradin zuciyarta ke ciki Da kyar samir ya samu ya talafo shi , still jikinsa na barin ya kawo shi saman doguwar kujera ya kontar ya kama takalmansa sau ciki ya cire masa ya bar masa safar ya saka hannu da sauri yana lalubo waya yana kokarin kiran likita Hannunsa na mugun bari ya dago jajayen idannuwansa ya sauke a kan Samir dake kusa da Aisha wace ke kuka bilhaki tamkar iyayenta ne suka mutu🤦‍♀, murwa na rarabe masa ya ce" *SSSAM...IR, SAMIR, MATA CE👉* cike da tashin hankali Samir ya juyo wajen Aisha ya ce" ki kira min number likita plz, Shi kuwa ya shiga yi masa fifita duda irin sanyin ac din dake office din Tana kiran likitan ba.a dauki lokaci ba sai ga shi da wata nurse rike da akwatin kayan aikin nasa sun shigo Suna shigowa suka bukaci su basu guri dan haka Aisha da Samir suka fito Suna fitowa Aisha ta nufi office dinta, daidai Rauda ta biyota su shirya dan kuwa idan ta biyewa Aisha sai su yi ta fushi haka Tana shigowa coridor dinsu ta hango Aisha na tsaye tana kuka tun karfinta Zuciyarta ne ta buga, ta daga kafarta da sauri ta karasa wajen Aisha ta dafa kafadarta ta ce" Aunty, mai ke damunki haka? Baki da lafiya ne? Mai yake faruwa? Aisha cike da tashin hankali ta riko hannun Rauda ta bude idannuwanta ta sauke a fuskar Rauda ta ce" mai ke damunsa ne? Mai yake hadasa masa cuta irin haka ne? Wacece ya ambata da *Mata*? , shin yana da aure ne? Idan yana da aure bai yi min adalci ba domin ni nafi kowa son sa, ni nake sonsa ba wata ba, ya dace ya kula da ni, ya gane so yana iya halaka ni Lallana Ta karashe tare da rushewa da kuka Samir da yake kai kawo ya ja ya tsaya cak, bai san lokacin da ya dora hannayensa biyu saman kansa ba cike da tashin hankalin da yake hangowa Murya kasa kasa ya ce" *wata rayuwar.......* I.m sorry nah, typing din dan lokaci ne, kuma bakwa comment balatana na ji ina ai sai na yiwa readers typing😇😇 *❣IDAN KA RAINA INDA KAKE❣* 1⃣2⃣ Na: *SAJIDA* *_🌈KAINUWA WRITERS✍🏼 ASSOCIATION_*🤝🏻 ```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}``` https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation Rauda ta hadiyi wani yawu mai zafi, ta rike hannun Aisha ta ce" ki kontar da hankalinki aunty, du abinda koncin hankali bai bada shi ba tashinsa ba zai bayar ba, Aunty plz ki nutsu mu je office din ki Girgiza kanta Aisha take ta ce" ba zan iya tafiya ba tare da na ga halin da yake ciki ba, ki tsaya su fito mu je mu ga jikinsa Ajiyar zuciya ta dawo saukewa domin bata ga ta inda zata bi ta kontarwa da yayarta hankali, wannan lamari sai dai du.a.i kawai Samir da ya gama kalonsu cike da tashin hankali, domin sai yanzu ya gane inda lamarin ya dosa, a hankali yake taka kafafuwansa har ya koma office din Sudais wanda likita ya gama dubasa ya zauna yana yi masa magana kamar haka" Elhaj Sudais, ka kula da lafiyarka , ka kiyaye abubuwan da ke jefa ka a irin wannan hali domin idan ana haka za.a iya yin barna.... ita zuciya da ka ganta idan ta fara nuna irin haka abinda ya fi dacewa shi ne a kiyaye, a tatale ta, a raba ta da dukan abinda zai kasance izgili wa ita, Kafin ya karasa magangannunsa Sudais ya dago ya sauke idannuwansa a kan Docter, bayan docter ya hango samir na tsaye shima yana sauraron abubuwan da likitan ke fadi sai gefensa na hagu nurse din ce ta mayar da kayan tana jira su fice Murya kasa kasa ya ce" har yanzu tana can ko? Da sauri Samir ya karaso ya dafa kusan hannunsa ya ce" aa, ta shigo daman dan acaba ne Da yannayin bacin rai Sudais ke kallon samir a kasan zuciyarsa ya ce" Acaba? Acaba fa ka ce? Daman *MATA* na hawa acaba har ya taba jikinta? Daman tana yi min irin wannan gangancin? Shin yaushe *RAUDA!* zata fahimci abinda nake nufi da ita ta furta abinda nake jira daga gareta mu shige rayuwar da nake mafarki nake fata? Du wannan magangannun yana yinsu ne a cikin zuciyarsa inda Samir ya ci gaba da fadin " suna kofa suna jira docter ya fito su shigo ganninka Dagowa yayi da sauri jin knocking Kafin yayi wani yunkurin har Samir ya bada izinin shigowa Kansa ya mayar ya lumshe idannuwansa yana jin yanda bugun zuciyarsa ke karuwa Aisha ce gaba Rauda na bin bayanta a tsorace domin sam bata son abinda zai kuma hada ta da wannan mutumi, ita dai bata san dalilin da ya sa take tsoronsa ko dan ya kasance mai akoy sannan mai gidansu a wajen aiki ne? Sai marin da ya yarfawa Aisha har yanzu idan ta rintse idannuwanta yakan sakata saurin budewa domin wulgawarsa kawai take gani Tsayuwa suka yi, mirya kasa kasa Aisha ke tambayar jikinsa, inda daga inda Rauda take ta dan tsura masa ido, a ranta take fadin" lale wannan bawan Allah dole ya ringa wulakanta yan matan da suka je gare shi domin Sudais kallo daya zaki yi masa idan dai kina da cikakiyar lafiya ki yi fatan samunsa a matsayin miji Ga kudi ga kyau dole mata su yi haukansa Dan bakinta ta murguda a ranta ta ce" ba duka yan mata ba domin ni a nan ban ga abinda za.a tarba a zubar da mutunci ba Samir ne ke amsawa Aisha duda du ya daburce ya rasa ta ina zai bi Rauda ta tambayi uban masu gida da jiki.ba dan kuwa du yanda aka yi hakan zai.sanyaya masa zuciya Matsawa yayi gefe yanda zasuna ganinsa da kyau ya ce" ku karasa ku yi masa ya jiki mana? Aisha cike da farin ciki ta ja hannun Rauda sai kusansa suka ja suka tsaya inda Aisha ta yi masa ya jiki, Bai amsa ba, sai adu.a da yake yi kar ya mike ya tataka su a wajen nan dan kuwa kowace cikin su haushinta yake ji Muryar Rauda ta daki dodon kunensa ta ce" sannu Allah ya baka..... Bata kai da karasa maganarta ba ya bude idannuwansa tar a kanta, fuska a hade, ya zabga mata hararar da ta kada hanjin cikin su ya ce" get out f my office! Da sauri Rauda ta rintse ido jin yanda maganar tasa ta karade office din da wannan muryar tasa mai kama da amon zaki, Bata gama tantance a inda take ba muryar ta kuma razanar da ita inda ya firfito masu da idannuwansa ya kalo su gaba daya ya watsa masu kallon kyama ya ce" i said ku fice min a ofiice ko bakwa jin sautin murya ne? Da sauri Raudat ta juya ta fice Aisha ma ta biyo bayanta Basu zame ko.ina ba sai office din Aisha, Rauda na shiga ta zarce ta dauko ruwan sanyi cikin frij ta bude ta sha sannan ta shiga sauke ajiyar zuciya, Bata san lokacin da ta ce" tap, wannan mutun akoy jikeken kawai, gaskiya masu zama kusa da shi suna shan masifa duba fa ki ga yanda yake lumfashi da daydaya aman ya iya ya dakata ya masifaci mutanen da suka shiga dan yi masa sanu Ra karashe tana dafe kai Aisha ma murmushi ta yi ta ce" ai banbancin nasa kenan da wasu gajojin, kin san yanda yake yi mana na ban sha.awa hakan na nunin bashi da fade faden mata komai kyansu Rauda ta tabe baki ta ce" uhum, aunty wly ni ban ga abin birgewa a wajen wannan gabjejen, kin ga idan Allah yayi aurenki da shi idan alkhairi ne, koda na ziyarce ki to fa sai baya kasa dan kuwa wannan mutumin bashi da wani fara.a Aisha ta yi dariya domin ta lura Rauda iya gaskiyarta take fada kenan, ta mike ta nufi tatara takardunta a ranta tana fadin" an kusa, dan kuwa yauma ya kuma sauke idannuwansa a fuskata, Ta lumshe idannuwanta ta ce" Namijin duniya kallonka mai tafe da harara....... Allahu Allahu La ushirika bihi shai.a.... shine adu.ar da Sudais yayi ta nanatawa a wannan koncin bayan korar su Rauda da yayi, Gefensa Samir ne zaune a kujerar nan mai juyin mutun guda, ya zubawa abincin da aka kawo wa Sudais aman ya ki ci.. Tunani ne ya sako shi gaba, ya rasa ta ina zai kamo wannan lamari, wai dama *AISHA* ke son ogansa? Shi kuwa ogansa ga dukan Alamu ba Aisha ce ke jan ragamar zuciyarsa ba Ajiyar zuciya ya sauke ya juyo wajen Sudais ya ce" Elhaj, Sannin ba zai amsa masa ba, ya ci gaba da maganarsa dan kuwa ya san in dai ya ji koda bai bashi amsa ba ba zai yi masa karya ba, Ogansa baya shakun magana da kowa kai tsaye ya fada masa gaskiya Samir ya ce" oga mai zai hana ka tunkari matsalar nan da kanka ne? Ina nufin ka tunkareta ka fada mata damuwarka? Sudais ya dan bude idannuwansa ya jima yana kallon ac din dake daidai kansa , kamar ba zai yi magana ba kuma can ya ce" mai kake nufi? Samir ya bayar da hankalinsa sosai ya ce" ina nufin oga damuwar nan tunda har ta fara kawo ka haka mai zai hana kawai a fada mata ta amince a yi komai a gama ko hankalinka zai dawo waje guda? Idan ka yi duba da wannan rashin lafiyar da ta fado, da irin yanda harkoki suke sanya, Elhaj baka taba zuwa gari ba ka shigo kampani baka yi zagaye ba sai wannan karin, kar ma.aikata su ankara su fara kokarin kawo sanya a harkar neman nan Dan tsagaitawa yayi da maganarsa yana adu.ar Allah ya sa bai bata masa rai ba, kai koda ya bata masa sai dai yayi hakuri domin bai ga wa zai fada masa ba, shi kam yana mamaki mutun kamar Sudais yana tsoron mace? Tsoron mace mana sai dai yana labewa a bayan kar ta raina shi da wasu kudiririkansa nasa, harma abin na kokarin jan dama dan kuwa yana hango rigima yana tsoron ka ja na ja ne za.a yi a wannan lamarin Jin shiru ya sa Sudais ba tare da ya dago da kansa ba ya ce" ci gaba Samir ya dan daburce, can dai ya ce" daman oga bana son abinda zai saka ka yi kasa ne, aman ka yi hakuri Sudais ya yi dan murmushi, ya sauko kafafuwansa kan takalminsa ya tsurawa Samir ido, a ransa yake fadin" kennan har ana gannin feeling dina a kan wannan yarinyar haka? Har an gane halin da nake ciki? Ko da yake shi ai shi na saka aikin ya bibiyar min ita dole ya fahimci halin da nake ciki...., sai dai kash koda zan zube sau dari ne saboda damuwarta ba zan yarda na barar da kaina kamar yanda kake so Samir ba, naki din, ba zan amince da shawararka ba Aman a fili ya ce" a dukan jawaban da kake kana nufin ina son yarinyar nan ne ko me? Shin Samir na taba yi maka maganar ina sonta ne? Samir ya dago da sauri da mamaki shinfife a fuskarsa, lale ma ogansa yana kokarin ya take maganar kenan, a hankali ya girgiza kai Sudais yayi murmushin gefen baki ya ci gaba da fadin" a iya sanina nakan kirata da *MATA* ne kawai, mata kuwa yana da ma.ana biyu mata kamar yanda ake fadi sai kuma mata ana nufin *Matata* Iya nazarin hangena ban bambance maka wane nake nufi ba _rashin lafiya kuwa Allah ne ya kawota ba wai wata damuwa ba🤦🏻‍♂ _a kadan mun yi shekara biyar da kai, ina tunanin kai ne wanda ya fi sannin sirina bayan yan gidanmu dan kuwa koda a jarida na boye wani kai kam na fada maka duka dan ka natsu ka daina gannin ka tashi a gidan masu kudi ka ce zaka yi wasa da damarka har chance dinka ta kubuce maka Ya kuma yin murmushi ya ce" ban ce aa ba, kuma ban ce eh ba, ban ce na isa ba kuma ban ce ba zan iya yakiceta a lamurana ba, ban ce da kai ina sonta ba, kuma ban ce da kai na tsaneta ba, ina so daga yanzu a daidaita su da sauran ma.aikatana, ina so yanda za.a hukunta kowa a hukunta su idan suka taka dokokin ma.aikatata, ina so a yiwa Babar gargadi na kirki kan abinda ta aikata na taran gabana ta firtan banzar maganarta kan idan ta kuma za.a koreta, ina so na karyata abinda ya faru da ni a yau sannan ya zamo sirri, zan yi zagaye ranar litinin karfe bakwai da rabi ina so kowa ya halarta a farfajiyar ma.aikatana banda masu tsaro kawai, Samir kar ka manta wanda Maciji ya sara koda ya ga igiya yakan tsorata ne, kana iya tafiya! Samir ya mike, cike da jin dadin ogansa zai dawo yanda yake (🤣) ya juya har zai fita sudais ya ce" SAMIR Ya ja ya juyo, Sudais ya ce" *SAMIR INA SON TA!, Aman hakan in sha Allah ba zai kayar da ni ba!* Ido Samir ya zaro na mamaki ya ce""" *❣IDAN KA RAINA INDA KAKE❣* 1⃣3⃣ Na: *SAJIDA* *_LITATAFAN MARUBUCIYAR_* *_Duk Karyar kasa_* *_Yar Mahaukaciya_* *_Neman na kaina_* *_Bani da zabi_* *_Idan ka raina inda make_* *🌈KAINUWA WRITERS✍🏼 ASSOCIATION*🤝🏻 ```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}``` https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation Bai barshi yayi maganar ba sanadiyar hade girarsa da yayi Da sauri samir ya juya yana magana da zuciyarsa yana tsananin mamakin lamarin Sudais Mikewa ya yi ya karasa gaban table din yana dan langi domin har zuwa lokacin bugun zuciyarsa ba wani daidaita ta yi ba Agogon hannunsa na azurfa da suka konce ya dauko ya daura a hannunsa na hagu, ya konce hiraminsa ya shaki iska ya sauke ajiyar zuciya a ransa ya ce" soyayarki a cikin zuciyata gaskiya ce, tashin hankali wa wannan soyaya wajibi ne, abinda yake kila wa kala kankaruwar soyayar taki daga zuciyana, wannan shi ne nake tunanin zai yiwu kuwa? Sai dai na fahimci karfina isata wayona ba zai bani wannan dama ba, aman zan fadawa Allah ya cire min wannan bakon lamari dan kuwa ya girmami tunanina *Mata*, ina so Allah ya sa kar wannan soyaya ta taba lafiyata harma ta sa na shiga hakin mutanen da nake tare da su, Zan yi hulda da ke ne kamar yanda zan yi da sauran, *Mata* zan cinye wasan ta wajen daina son ki Ya karashe maganar yana mai sakin dan guntun murmushi kafin yake zama kan kujerarsa ya jawo takardun da ya dace ya duba tun safe ya shiga aikace aikace bilhaki ( agogo kennan sarkin aiki ) Eyah, *Jarina* ya jikin nasa yanzu? Nana Mariama ke tambayar Aisha dake zaune tana fada mata irin rashin lafiyar da yayi yau a office Aisha ta ce" uhum, mama na tsorata, na ji tsoron kar a je ya mutu *burina ya kasa cika* Da sauri Rauda ta kalo wajenta, bata san lokacin da bakinta ya furta" aa🤔, Aunty daman kukan nan da kike rusawa ba na soyayar nasa bane? Aisha ta kalota ta yi murmushi harda juya ido, ta ce" kina da matsala Lalla,, kin ga ai yaro da kudi akewa kirari ba wai gardi ba, ina son SUDAIS sai dai da kudinsa na fi son sa! Rauda ta ci gaba da ninke kayansu tana sauraron hiraraki har suka zo inda ya kore su irin tsoron da Rauda ta ji Nana Mariama ta yi ta dariya tana kallonta ta ce" oo, Rauda Allah ya shirye ki ke kam Itama murmushi ta yi tana kara hango fuskarsa da irin hararen da ya zabga masu du dan kawai sun yi masa sanu a ranta ta furta" ina tsananin tausayin mutanen da yake mu.amala da su, ina tausayin kowa ciki harda matarsa shi yasa nake tausaya maki auntyna Tana gamawa suka shiga shirin dora tukunya dan kuwa weekend ne, aman kowace a kasan zuciyarta tana zulumin abinda zai faru ranar litinin da aka ce za.a hadu a tsakar ma.aikatar cikin shukoki Yau lahadi, tunda yama yake bangaren Hajiya kaka, sun sha hira kamar kulun har lokacin bacinsa ya kusa dan haka ya mike yayi tafiyarsa aman ya manta wayarsa a nan Hafsat dake zaune ta dauka cike da murnar zata turi kudi yau ta shiga ta tura, bayan ta gama sai ta yi sha.awar shiga hotuna dan ta yi kallo Kalo take sha du yawanci na kalolin kayayakin da yake siyarwa ne irin wa.inda da an bugo sabin kala ake turo masa a yanzu da ya taho daga saudiyar da kuma idan baban harka ta samu ta gold da ake turo masa hoto dan ya fara gani kafin a je a auna Ta shagalta kayayakin sun birgeta sosai sai kuma ta fito ta shiga wani dossier din wanda a cikinsa kuwa hotunan yara ne, kyawawan yara yaran larabawa, yaran hausawanmu, yaran turawa bulbul da su , haka kawai ta ji tausayin yayan nata ya darsun mata a zuciya Ta fita sai ta ga wani dossier shi kuwa an rubuta *MATA* Maimaita sunnan ta yi, sai hakan ya bata a kwakwalwarta mata ko kayan mata ne irin sana.arsa Ba tare da tunanin komai ba ta shiga, Mamaki ne ya kasheta a zaune, ido ta shiga tsurawa hotunnan nan, wani waje yarinyar ta fito daga aji, wani waje ta tsayar da adaidaita, wani wajen zata shiga wani gida, wani wajen tana hira da yar uwarta suna shan dariya irin ta yi murmushi Mamaki ne ya kashe hafsa a zaune, ta yi tsai tana kallonsu, fuskokin nan nasu kamar ta sani aman a ina ta san su? Sannan mai ya hada hotunan nan da yayanta? Mai kalmar *MATA* take nufi? Kanshin turarensa ya isar mata da sakon zuwansa wajen da take, dan haka da gagawa ta fita a wajen tana kokarin bude wani wajen ta dan dago ta saci kalonsa Tsaye yake ya harde hannayensa yana kallon kanwar tasa, a ransa yana mamakin irin yanda bata tsoronsa take aikata abubuwan da ya hana, Hannunsa ya mika mata kawai ta sako masa wayar ya juya yayi tafiyarsa Ajiyar zuciya ta sauke ta mike tana tunani, a kasan zuciyarta tana fatan All3 ya sa haka ne, da kuwa ta fi kowa murna yayanta ya kamu da so ko menene? . Ranar monday Rana ce da aka tashi da lumshin hadari, safiya ce mai cike da ni.ina Lunlumin nan ya saka du ake gannin tamkar safiyar bata gama wayewa ba , Karfe bakwai da rabi du wani ma.aikaci ya halarta a harabar jardin din da zasu yi meeting Aisha na tsaye kanta a kasa, du irin gyaran fuskar da ta sha ta goge shi da ruwan hawaye sakamakon kiranta da aka yi da zuwansu aka wanketa tas tare da kwakwaran kashedin idan ta kuma aikata abinda ta aikata za.a koreta a ma.aikatar tare da fita hakinta na iya adadin aikin da ta yi masu a ma.aikatar sannan aka canza mata waje tare da fadin bata cancanci wannan waje ba Rauda na kusanta tana tambayarta lafiya? Kasa kasa aman Aisha ta yi shiru ta kasa bata amsa Wajen kuwa ya cika da tsararun ma.aikata, yan mata sai gwali ake an sha kyau sosai da sosai, Samarin ma du sun sha cost matan aure sun sha lulubinsu masha Allah, wajen ya hadu da dan duhun hadarin nan yana bayar da dan gumi gumi sanadiyar daurewar da hadari yayi sai kanshin turaruka kala daban daban ba wari a al.amarin Salif kuwa da sun hada ido da Rauda zai sakar mata mirmushi ne mai sanyi ita kuwa sai ta sada kanta kasa tana dan murguda bakinta tana fadan kallon yayi yawa Suna haka ya fito ta kofar dake kallonsu, a yau yayi shigar hausawa ne, ya saka shada kalar ruwan baki ya dora hula ruwan zaren da aka yi masa aikin shadar sai takalmi kafa sau ciki baki na fata Gaba daya da kallo suka bi shi, ya hasko wajen dalilin kalar fatarsa da ta yi luwai luwai tamkar ba rana a kasar Yana tsayuwa guard dinsa biyu suka tsaya a bayansa wanda daya ne kawai ake iya hangowa sayan kuwa fafadan kafadun Sudais sun kare shi kwatkwatA Da sauri adjoin dinsa ya mika masa farar takarda doguwa bayan ya risina Karba yayi ya dan duba, ya dago ya cire dan siririn bakin gilas din dake idannuwansa Murya kasakasa, ya furta " ASALAMU ALAIKUM" Da ba dan yar lasifikar😌 dake sakale a kunansa ba da ba wanda zai iya jiyo shi domin yawan mutanen da kuma yar tazarar dake tsakaninsu Ci gaba yayi da magana kamar haka" du wani ma.aikaci na gidan ya san rules din mu, du wani ma.aikaci kafin a dauke shi sai an bashi takardar yarjejeniya ta kulawa da aikin da ya kawo shi idan kuwa ya taka mana dokoki da irin hukuncin da ya dace da shi An gina Abaya nd Gold kampani ne bisa abu daya! Shi ne *NEMAN KUDI* A cikin rules din gidan nan wace zan kuma nanata maku shi ne ba sani ba sabo, idan kana da damuwa ka zo ka tarar da ni, idan barin aiki ne da ni zaka yi magana, ko wata iri ce damuwarka ni zaka zo ka gani Ya karashe da nuna kansa wanda hakan ya baiwa sauran damar dagowa suka kuma kalonsa dalilin kwarjinninsa da haibarsa ya sa suka furta *MASHA ALLAH* ya ci gaba da fadin...... *❣IDAN KA RAINA INDA KAKE❣* Na: *SAJIDA* *_LITATAFAN MARUBUCIYAR_* *_Duk Karyar kada_* *_Yar Mahaukaciya_* *_Neman na kaina_* *_Bani da zabi_* *_Daga tafiya daukar soja_* *_Idan ka raina inda make_* *🌈KAINUWA WRITERS✍🏼 ASSOCIATION*🤝🏻 ```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}``` https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation 1⃣4⃣ Ya ci gaba da fadin" an samu canje canjen poste da aiki, domin an tace an tantance kowa irin aikin da zai yi dan haka du wanda aka ba aikinsa sai ya bada hima ko ya rasa dan ba zamu yi sanya da aiki ba kampani ya samu matsala Ya jima da yin shiru ya ce" du mai matsala da hakan yana iya samuna ni ba mataimaki ba wani ba, Ma.asalam Yana gamawa ya ajiye takardar da aka rubuto bai karanta komai ba, guard dinsa daya ya dauka suka bi bayansa Yana shigrwa kowa ya ksma gabansa ya nufi ma.aikatarsa Su Rauda na zuwa suka shiga aikinsu suna hira tsakaninsu cikin raha da mutunci Shigowa mataimakin Sudais ya yi , bahaushe ne bakin mutun dogo mai sunna sidik, yana zuwa suka gaishe shi Amsawa ya yi da yar fara.a dan kuwa akoy fahimtar junna a tsakaninsu Takarda ya mikawa Rauda ya ce" ki saka hannu a nan na kaiki wajen da aka canza maki Ido ta zaro , su basma kansu nan da nan suka hade rai suna kallon juna domin kuwa sun yi sabo harda na mamaki, dan kuwa suna zaune ne da fahimtar juna ana mutunta juna a yi wasa da dariya Jiki a mace ta dauko pos dinta ta mimika masu hannu tamkar ba zasu kuma haduwa basma ta dan rumgumeta irin gaisuwar larabawa sukai salama kan sai sun hadu lokacin cin abinci ta bi bayan Sidik Yana gaba tana biye da shi a baya, abin mamaki sai gasu a office din Aisha, da sauri ta kale shi da alamun karin bayani Ya ce" nan ne sabon office din ki, sai ki maida hankali a aikinki banda wasa idan kika yi wasa da damar nan za.a canza maki ne dan kuwa wace t fita ta yi wasa da damarta ne so be careful Tana kallonsa tamkar sakara har ya fice bayan ya gabatar mata da litafin program din aikinta daga litinin har juma.a Sai can ta yi firgigit ta zazaro idannuwanta waje, hannayenta biyu ta dora a kanta ta furta" ina ba zai yiwu ba, nan fa office din aunty ne, aman ina take ita auntyn? Ina aka mayar da ita, mai ta yi? Ko shi ne sanadiyar fushinta? Ya Allah ka shige min gaba ka fi kowa sannin aikin nan dan me nake yin sa, ka fi ni sannin abinda ya dace da rayuwa ya Allah kar ka bar wata fitinar ta kunno tsakanina da aunty a sanadin wannan waje , ka sa wajen da aka kai ta ya fi yi mata dadibkan nan Ta jima kafin take daukan litafin, dan kai kawo ta shiga yi tana karanta abubuwan da suka zama wajibi ta yi a kulun Ajiyar zuciya ta sauke ta kai dubanta wajen takardun da sai ta bi daya bayan daya na office office ta duduba rubutun da aka yi ta karanta sannan ta kai office din oga ya sa hannu ta dawo ta bi office office ta rarabawa kowa, haka zatana yi ko wace safiya kafin ta dawo amsa kiran masu bugowa dan yin magana da oga idan ya zama wajibi su yi magana ta kai masa idan kuwa bai zama wajibi ba ta karbi bukatar mutun ta bayar da order a yi, aikin Rauda dai baban aiki ne wanda mafi akasarin masu malakar wajen nan sai sun karanci abin, sannan sai mai hazaka da hakuri Cikin gagawa ta shiga dubawa sai dai du gagawanta bata samu ta dube gaba daya takardun ba gannin ta dora lokaci sosai ya sa ta saka farar takarda a tsakiyarsu ta mike ta gyara zaman hijabinta ta dauka ta yi office din Sudais Zaune yake yana amsa kira a waya, magana suke da mahaifiyarsa ya bada nutsuwarsa gaba daya Rauda kam tana zuwa ta dan yi knocking , Tsai yayi ya zuba mata ido ta cikin computer, har sai da mamansa ta maimaita kana ji na kuwa? Sudais ya sauke ajiyar zuciya ya ce" eh mommy , yanzu du yanda kike so a yi a yi kawai Ta yi murmushi tana fadin daman na fadawa abanka baka da gardama kan wannan tsarin ba zaka fara ba Tana gama fadar hakan ta kashe wayar shi kuwa ya mika hannunsa ya dana abinda ke saman table dinsa wanda ke aiki da kofar wanda sai ya danna shi kofar ke buduwa Da salama ta shigo kanta kas, tana matukar jin tsoronsa da kwarjininsa haka kawai bata iya sakewa da shi har mamakin karfin halin yayarta take ganni da ta iya tunkararsa da kalmar "SO Tana zuwa ta gaishe shi da turanci ta gabatar masa da takardun Sai da ya duba agogon dake daure a tsintsiyar hannunsa na hagu ya dago fuskarsa a hade bai ce komai ba ya amshi takardun ya shiga saka hannu Yana tsaka da sakawar ya zo daidai farar takarda, ya dauka ya shiga jujuyawa ya dago yana kallonta , har zuwa lokacin bai furta mata kalma ko kwaya daya ba Idannuwansa da suka sauka a fuskarta suka saka ta shiga halin daburcewa dan kuwa sai ta shiga dan sosa goshinta da yatsutsanta na dama har wani dan gumi ya fara karyo mata Inda indar da bata san tana da ita bace ta same ta lokaci guda ta ce" am am am.....daman su na kasan nan ban karanta ba domin ina tsaka da karatun na ga lokaci ya kure kar na yi laifi shi ne na kawo maka su haka dan na san ai ba zaka saka hannu a iya karatuna kawai ba Tunda ta fara magana ya tsare lebenta da kalo, wanda idan har ba tsayawa ka yi ka kare masa kalo ba ba zaka fahimci shi din yake kallo ba, tamkar mai hararan fuskar nata, da zuciyarsa yake kokowa yanai wa idannuwansa fada kan ba kyau irin kallon nan aman ya kasa kauce idannuwansa, Dago da idannuwanta ta yi a dan tsorace jin yayi shiru, sai ta ga harararta ne yake ashe, da sauri ta kuma sada kanta ta hade hannayenta tana wasa da su Da kyar ya aro jarumta tunawa da yayi abinda yake son yi wato yakice ta a ransa, cikin dakakiyar mirya ya ce " kin san mai ya kawo ki wannan ma.aikata kuwa? Da sauri ta daga kanta gabanta na faduwa tana tsoron ya kore ta, Ya ci gaba da fadin a wani waje kika yi stage ne? (Sarai ya san bata yi ba) Da sauri ta dago, hankalinta ya fara tashi , bakinta ya shiga rawa dan kuwa ita ba karya zatai masa ba aman kuma tana tsoron gaskiyar ta haifar mata da matsala, shi kuwa yayi shiru da dukan alamu sai ta bashi amsar zai saurara mata A hankali ta ce" ban yi stage ba What ? Ya fada da dan karfi yana mai dan fitar da idannuwansa, ya dafe goshinsa da yannayin takaici ya ce" ki saurare ni da kyau, nan ba wajen ki zo ki koyi aiki ba ne, wajen ki zuba basirarki ne ki yi aiki tukuru, takardun nan ki koma ki karance su , ma.anar ki fara karantawa dan koda da wani abinda bai dace ya karaso wajena ba ki cire idan kuwa baki fito da niyar aiki ba sai ki kara gaba Sauraron tsagwaron rashin mutuncin wannan bawan Allah take, mamaki fal zuciyarta to aman meye laifi dan bata iya aiki an koya mata ba? Cikin sauri ta shiga tatarewa hannunta na rawa ta juya da sauri ta koma office dinta, wato dai lokacin da ya dace ta je ta ci abinci sai ya kasance ta kare shi a aiki A wannan ranar bata gama aiki ba sai da ta yi yama sosai ta fito a office din inda ta ga sai yan tsiraku Neman Aisha ta yi bata ganta ba ta juya ta kama hanya ita kadai Tana shigowa gida magariba na kawo kai, ta shigo da muguwar gajiya har juwa take gani sai dai kafin ta rufe bakinta da salamar da ta yi sai ji ta yi an dauketa da mari Da sauri ta kallo mai marin, Mamaki shinfide a fuskarta, Muryar mahaifinsu ce ta katse mata mamakinta yana cewa" Aisha, Aisha ina yi maki hani da saurin hannu, tabas kece yayar Rauda aman ki kiyaye saurin bugu sannan yanzu na gama fadar ki yi hakuri ta zo na ji ko? Murya a raunane Rauda ta ce" Aba me na yi? Mahaifinsu ya ce" Rauda, ya aka yi kika amince da wajen da yar uwarki take so bayan kina da zabin kin karbar aikin? Cike da mamaki take kallon Aisha, dama saboda wannan aikin ta zabga mata mari haka? Bata gama tunaninta ba Aisha ta ce" ta fada min daman tana daya daga cikin masu bakin cikin wannan waje nawa ko me? Daman idan na hau abu na sauka zaki hau shi Rauda? Mai na yi maki da zaki yarda ki yi aiki a kusa da shi, a tunanina koda korarki za.a yi ba sai dai a kore ki ba? Shi ne aka kai ki wajen da nake aka kawo ni wajen da kika bari cikin matan da suke tunanin kanmu daya da su? Du sai na sa ya kore su daya bayan daya, sai na zame masu barazana a aikin su, domin ni na fi karfin su ! Tana gama fadar haka ta juya ta shige ranta a bace, mahaifiyarsu kuwa ko kanzil bata ce ba alamu dai itama tana goyon bayan abin Murmushi mai ciwo Rauda ta saki, ta kali mahaifinta ta ce" ka yi hakuri Aba , insha Allahu gobe zan je na ajiye aikin dan samun farin cikin kowa a gidan nan To readers shin ta ajiye aikin ne??? *❣IDAN KA RAINA INDA KAKE❣* Na: *SAJIDA* *_LITATAFAN MARUBUCIYAR_* *_Duk Karyar kada_* *_Yar Mahaukaciya_* *_Neman na kaina_* *_Bani da zabi_* *_Daga tafiya daukar soja_* *_Idan ka raina inda make_* *🌈KAINUWA WRITERS✍🏼 ASSOCIATION*🤝🏻 ```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}``` https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation 1⃣5⃣ Cike da tausayi ya bi ta da kallo, shi kam bai san yaya zai yi da wannan lamari ba kuma du bai gane inda magangannun Aisha suka nufa ba, aman ba komai ya tabata Allah na tare da mai gaskiya Sukuku ta yi komai, ko abinci kasa ci ta yi ranta a bace ta yi mamaki da Aisha ta biyo ta wannan hanyar ta fadawa iyayensu, to aman ita bata da tunani ne? Ta ya ma.aikatar da ba ko sisin dalarta za.ace wai tana da damar ta ce a canza mata? Idan har hakan ne ai da itama sai a ce tana da damar cewa nan take so ba zata bar wajen ba ko? Baci dai sai barawo ya sace ta, tana tunanin idan kudin da za.a bata basu kai na biyan makarantar nan ba fa yaya zata yi kennan? Gannin ba barcin zata samu ba, sai kawai ta dauro alwallah ta yi nafilolinta ta zauna ta yi ta adu.a kan Allah yayi mata zabin abinda yafi zama alkhairi a rayuwarta Da safe ma da wuri Aisha ta yi tafiyarta du irin saurin da ta yi dan su tafi tare bata tsaya ta ba Tana fitowa ta gaisar da mahaifiyar su A dakile ta amsata dan tun jiya take jin haushin wai ita da take kanwar Aisha maimakun ta taya ta yakin soyayar wannan mutumi ko sa warke da wannan bakin talauci aman aa ita ce ma ta amince da hanyar da zata kusanta yar uwarta da warakar su Jiki a sanyaye ta ce" umma zan tafi Amsata ta yi da A sauka lafiya Fuskarta ta kure da kallo, can ta juya ta fita Kwata kwata kudin hannunta naira dari da hamsin ce, itama tsohuwar ajiya ce da ta yi dan irin wannan rana domin idan ran su ya bace bata ba ta kudin mota Bos ta shiga , ita ta kai ta ma.aikatar wace a yau bata zo da niyar yin aiki ba ta zo ne da niyar tambayar salama Tunda ta zo take zaune ta gama duba takardu ta je office din sa ya fi a kirga sai dai baya nan abin ya daure mata kai kuma ita bata ji an ce baya nan ba Tana zaune har lokacin tashi ya yi ta fito ranta a jagule tana cike da zulumin abinda zata je ta tarar a gidan ta kama tafiya cikin sauri dan kudin su isa kaita bakin titi Humaira ce take mikowa Sudais cofee sai turiri yake Fatiha ya shafa na wuridin da ya zauna ya yi, ya mike bai karbi cofee din ba ya juya ya koma saman table ya dan tatare rigarsa ya zauna ya daura kafa daya kan daya Da ido Humaira ta bi shi, a ranta kulun mamakin irin yangar Sudais take sai kace wata mace ko a me ya dauke ta tana tsaye har ya gama gyara zamansa sannan ta juya ta tarar da shi wajen table din ta dan risina dan ta san dalilin haka ya sa yayi kamar bai gan ta ba Karba ya yi ya ajiye saman table din kasa kasa ya ce " thanx (dabi.unsa kennan yakan godewa abin alkhairi yakan yaba kwaliyar matansa da sauransu....) Kujerar dake gefensa ta ja ta zauna, ta bude kulolin abinci ta zuba a plat daya , ta saka cokali biyu ( shima na cikin dabi.unsa, isan girkin mace ne zata tardo shi ne bangarensa ta gyara ta yi komai ta saka turaran huta dan kuwa du kudinsa bai amince yan aiki su yi aikin bangaransa ba , su dai matansa anai masu komai aman shi sai dai su yi, hakan na saka masu matsala da Humaira domin a kulun sai yayi fadan bayinsa bata wanke ba, zanin gadon da ya tashi a shi bata canza ba turare bata saka ba, wani lokacin sharar kanta bata samuwa sai daga baya ya gane kazanta ce kawai da ita sai ya yi hakuri ya shareta) Tana zubawa ta tura tsakan table din a hankali ta furta bismillah Ba tare da ta tsaya ya fara ba, ba wani dan rarashi, ba irin dan ta matsa kusa da shi kawai abincinta ta fara ci Tana gamawa ta zuba jus na kwali wanda su kadai suke shan abinsu, Sudais yana da son irin jus din natural aman baya samun hakan sai dai ya sha ruwansa kawai wani lokacin ne ma Khairat ke yin na kwakwa Tana gama sha ta mike ta fice ta yi bedroom dinsa dan canza zanin gadon (🤦‍♀) Ajiyar zuciya ya sauke bayan shigewarta, ya bi yannayin tsaruwar falonsa da kallo, a ransa yake fadin " to ko dai da ake cewa haisawa basu iya tatalar miji hakan ne? Dukiya ta gidan duniya Allah ya malala masa, sai dai kash ya kasa samun yanda yake so 100/100 Mikewa ya yi yana duban agogon dakin, karfe goma na dare ya nufi dakin Khairat dan gannin jikinta domin a yau rashin lafiyarta ya hana shi tafiya kampani, athmarta ne ya tashi da kyar aka samu ta konta A hankali ya tura dakinta ya shiga da salama Tana konce da doguwar bakar abaya, idannuwanta lumshe tana sauke ajiyar zuciya, sosai wannan rashin lafiya ke wahalar da Khairath, bata isa ta kwana biyu lafiya ba sai ta tashi hakan ya sa baya so yana nesa da ita dan Khairath akoy son ta kyautatawa wanda take tare da shi bale shi da ya zama mijinta, dan ma yannayin jikinta na hana ya wani abin aman ta san da bata da girman jiki da ya samu exactly irin kulawar da yake so A hankali ya duka kusa da gadon nata, ya tsurawa fuskarta ido, Fuskarsa ya matso daidai da nata, ya dan goga mata sajensa daidai lebenta dan ya lura bata ma san ya shigo ba A hankali ta bude idannuwanta, sai ya gan su sun yi fari kal kal harda wasu ruwa ruwa a cikinsu sannan sun dan fada A hankali ya shafi gefen fuskarta da hannunsa na dama murya kasa kasa ya ce" *YA KE MAR.ATUN SALIHA, JIKIN NE BAI DAINA CIWO BA?* Murmushi ta yi da jin sunnan da ya fada mata, ta dago hannunta da take ji ya yi mata wani mugun nauyi marar misaltuwa ta dora a kan nasa na dama ta ce" yayana, mijina, abokin rayuwa na Shi ma murmushin ya yi mata ya lumshe idannuwansa Bai zata ba ya ji ta ce" ba ka taba furtan kalmar so ba *SUDAIS*, ko zaka furta min na kwana da farin ciki a yau? Idannuwansa ya tsura mata ya kai minti hudu, suna yiwa juna kallon ido cikin ido, kokowa yake da zuciyarsa, fada yake yi mata kan ta daina irin haka har matarsa ta san bai taba furta mata kalmar so ba? Khairath ta cancanci soyayarka koda yar kadan ce dan haka ya sakar mata murmushi ya dafe hannayenta sosai ya ce" *KHAIRATH* sanninki alkhairi ne khairana, *ina son ki* Wani irin murmushi ta saki har da ajiyar zuciya, Kansa ya dan girgiza ya lakaci hancinta ya kai mata kis a goshinta ya ce" na yafe maki laifin yau da kulun da wanda na sani da wanda ban sani ba, Itama murmushi ta yi, wannan dabi.a da ta koya masa tanai mata dadi fiye da tunanin mai karatu, itama a hankali ta ce" na yafe maka laifin da ka yi min na yau wanda na sani da wanda ban sani ba, na yafe maka na kulun kukulun *mijina* kuma ina son ka sosai fa Shima murmushin ya kuma yi ya yi musabaha da ita ya ce" ki huta lafiya uwar Yayana, Allah ya tashe mu cikin hankalin mu Da amen ta amsa shi , ya juya ya tafi Sai bayan ya tafi ta share hawayen idannuwanta ta koma hannunta na dama ta yi adu.a ta shafa ta rufe idannuwanta da fatan Allah ya sa tana cikin masu rai A kadan ya dau minti talatin a dakin Khairath, yana shigowa wanka ya fada , yana gamawa ya saka kayan bacinsa ya yi bisimillah ya hau bed din sa Adu.a ya zauna yana yi sosai, bayan ya gama ya shafe ilahirin jikinsa yana kokarin kontawa Humaira ta shigo, Ta sha shirinta na barci wanda da mai gida ya gani zai rude ne, Bed din ta hau itama ta yi adu.a ta shafa ta konta ta dora kanta saman kirjinsa A hankali yake dan shafa gashin kanta, ya jima yana haka kafin yake kokarin fara isar da sakon sa wa ita Tsai ya tsaya, ya janye hancinsa a hankali ya dan shafa kanta da sigar da zata fahimta ya ce" Humaira Dan dago da kanta ta yi tana kalon sa dan ta san maganar mai mahinmanci ce, Idannuwansa ya lumshe tamkar ya rufe su, shi kuwa kure ta ne ya yi da kalo, ya ce" abin nan ya yi yawa Humaira, yana damuna da yawa, bana samun sakewa da ke domin ya kai ya kusan cinye kwayoyin dake baiwa fatarki kariya wanda idan ya gama cinye su baki kuma da inda zaki dafa ki dawo yanda kike, Farin nan ya isa haka, da ni kika bi da baki yi abinnan ba, dan kuwa bakin ki mai kyau ne Tunda ya faro maganar bleating din da take ta dan hade rai , ya fito ya gaya mata kawai wari take menene za yana kwana kwana da ita?, shi dai ya fiya takura ita kuwa a gaskiya bata ga abinda zai gaya mata ko yi mata ya hana ta shafa mn bleating ba! Bata iya ce masa komai ba dan ya hana ta daga muryarta sama da tasa, ita kuwa ta tabata a haka idan ta buda bakinta ba zata fadi alkhairi ba, sauke kan ta ta yi daga kirjin nasa ta yi konciyarta dan nesa da shi Shima gyara konciyarsa yayi, dan kuwa ba zai bata hakuri ba dan ya fada mata gaskiya tana nufin ba.a isa da ita ba kennan! Kamar yanda ya saba tashin wuri haka ya farka, ya dauro alwallah ya shiga nafifilunsa Sai wajen karfe biyar ya mike ya tAsar da Humaira ya fice yana mamakin ya aka yi Khairat bata fito ba Dakinta ya tura, ya yi niyar shigewa sai ya hango ta inda ya bar ta, saman doguwar gukerarta, sannan abin mamaki konciyar nan dai ne da ya barta ko har ta juya ta kuma juyowa? Matsowa ya yi a hankali ya mika hannunsa ya dan bubuga gefen da take konce Bata da alamun motsawa, ya shiga dan bubuga jikinta shiru dai Gabansa ne ya ji ya yi mugun faduwa dan haka da sauri ya juyota ...... ........ .......... ....... *❣IDAN KA RAINA IN DA KA KE❣* Na: *SAJIDA* *_LITATAFAN MARUBUCIYAR_* *_Duk Karyar kada_* *_Yar Mahaukaciya_* *_Neman na kaina_* *_Bani da zabi_* *_Daga tafiya daukar soja_* *_Idan ka raina inda make_* *🌈KAINUWA WRITERS✍🏼 ASSOCIATION*🤝🏻 ```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}``` https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation 1⃣6⃣ Faduwar gaban da rabonsa da ya ji irinta har ya manta, saurin taba wuyanta ya yi aman ina sanyi karai jikinta tamkar an saka ta a frij ne, idannuwanta da suke dara dara a dan bude aman ba.a hango bakin nan dake tsakiyar idannuwan, Hannayensa biyu ya dora a kansa, a fili ya furta" INNALILAHI WA INA ILAIHI RAJ.UNE, INNALILAHI WA.INA ILAIHI RAJ.UNE gannin kamar tana kalonsa ya saka shi yin karfin halin matsawa sosai kusa da ita ya yi adu.a da dan ruwa a gefe ya shafe mata ido hakan ya sa idannuwan suka rufe Kirayen kirayen sallah ne ya saka shi mikewa, ya dauko dardumarta ya shinfida ya kabarta sallah dan kuwa ya san ba zai iya fita haka ba Yana kai kansa sujada na karshe ya ji zuciyar sa ta karye, domin jinsa yayi tamkar jariri, ya ji wani irin kuka ya zo masa, ya ga idan bai fadawa Allah ba wa zai fadawa? Ya ji shi a gaban shugaban shuwagabanni, wanda shi ya ba shi Khairath a matsayin mata kuma a yanzu da ya karba sai ya ji yana bukatar kai kukansa ko zai ji sanyi, Sosai yake hawaye yana yiwa Allah godiya da irin wannan jarabawa ta yau, ya roki Allah ya ba shi ikon cinye jarabawar, ya karbi bakuncin matarsa ya sa Aljanna ta zamto makomarta, a cikin sujadarsa yake fadin" ya Allah, Khairath matata na yafe mata dukan kuraran da ta yi min da wanda na sani da wanda ban sani ba, Ya jima yana adu.a kafin yake dagowa ya yo tahiya ya salamce, Adu.a ya tsaya ya yi sosai kafin yake mikewa Table din dakinta dogo baki ya sauke shinfidar saman ya dauko shi ya ajiye ya koma ya ciko ruwa a bokici mai girma ya dauko moda ya saka, ya dauko turaren miski dake gaban madubinta mai yawan gaske, ya dauko auduga ya dauko tawul biyu sababi masu girma, jikinsa a matukar mace ya bude akwatinta dake ajiye ya ciro *SUTURAR KARSHE* a wajen da ta nuna masa a dinkin karshen da ta yi domin takan dinka wata ne idan ta kara kiba ko ta zube ya fito yana kara share hawaye Hannun rigarsa ya dan gyara ya samu da kyar ya dora ta saman table din domin nauyinta ya karu sosai abinka da gawa Niya ya dauka a cikin zuciyarsa kafin ya maida hankali cikin nutsuwa yana binta a hankali ya cire mata tufafinta ya rufe mata sirinta da tawul din nan wato *TUN DAGA SAMAN MAMANTA HAR ZUWA DAIDAI GWUIWARTA, IDAN KUWA NAMIJI NE DAGA SAMAN CIBIYAR SA SUWA DAIDAI GWUIWAR SA* , cikin nutsuwa ya saka hannunsa na hagu ya dago ta kadan ya san jingine ta da jikin sa ya dan dadana cikinta dan ya baiwa damar datin dake cikin ta fitowa, Bayan ya gama ya mayar da ita ya kontar kafin ya saka safar hannu a hankali ya wanke mata sirinta ya wanke du wani dati kana ya fara yi mata wankan sabulu, A hankali ya bi ta da sabulu ya wanke ta tas da ruwa yana yi yana karanta mata suratul yasine a cikin zuciyarsa Bayan ya gama yi mata wankan sabulu ya dawo ya bi ta ya yi mata alwallah (cikin alwallar ba.a zuba ruwa a baki sannan ba.a shaka ruwa a hanci sai dai a dan shafa) sannan bai wanke kafafuwan ba ya koma ya kuma yi mata wanka da ruwan zamzam ya fara wanke kan ta, ya wanke gefenta na dama har kafafuwanta ya dawo na hagu ma ya yi hakan sannan ya dora kafarta na hagu kan na damarta, ya yi dabara da kyar ya samu ya wanke mata bayanta sau uku, haka ya yi da dayan gefen ma Yana gamAwa ya dauko dayan tawul sin ya bi ta a hankali ya goge ta sosai har table din sannan ya bude miskin nan ya dan shafa mata kafin yake dauko suturarta wace zata kasance suturarta ta karshe 😭, lokacin da ranta ya sha yi mata tambayar dan me take yawan ajiyar likafani? Sai ta yi murmushi ta ce masa tanadin likafani ne dan bata san a ina zata kasance? Tana so idan ta same ta ta samu cikaken sutura, tana fatan ya suturta, sai yayi murmushi yace mata idan fa na rigaye ki mutuwar fa? Sai ta yi saurin rufe masa baki ta ce" ban san misalin da zan yi maka ba, ni dai na sani zan yi kuka sannan zan so na shirya ka dan na yi a hankali ina yi ina karanta maka suratul yasin sannan idan an dauke ka na zauna na yi ta karanta maka kul.huwa lahu ina nema maka sa.ar shiga kabari, na yi ta yi maka adu.a, sai dai ni na san sai na rigaye ka ko dan hukar nan da ta sanyo ni a gaba Sai ya girgiza kansa ya ce: jikinsa yayi A kulun ina fada maki cuta ba mutuwa ba ce rashin lafiyar ki ya daina tayar maki da hankali sai lokacin ki ya yi zaki mutu , Dan tsam ya yi yana karewa fuskarta kallo, tamkar ya kirayi sunnanta ta amsa, tamkar ya kama hannunta ta biyo shi, jikinta ya yi mugun laushi, bata da wata kazanta, yar kunfar fitan rai bata wari ba komai, Gawarta ta kasance gawa mai tsafta , Ya Allah ka sa makoncinta ya kasance haka da.iman Audugar nan ya cira ya saka mata a kofofin hancinta da kunayenta da bakinta Sannan ya gyara likafaninta ya suturce mata jikinta yanda ake yi Zuciyarsa bugawa take sosai, haka jikinsa ya dauki wani irin dumi idannuwansa sun yi hulu hulu fatar jikinsa ta yi jajajir irin yana cikin tashin hankali Turaran nan ya kara shafa mata a jikin likafanin ta ya yi tsai ya kuma tsura mata ido, a hankali ya ce" Khairath, Mar.atusaliha😭, Ni Sudais Mijin ki na yafe maki dukan kuraran da zaman tare kan haifarwa wanda na sani da wanda ban sani ba, ina rokon ki da ki yafe min nima, Khairath kin rasu ke kadai sai Allah sai mala.ikan da ya dauki aron ran da Allah ya baki Ina rokon Allah ya sa wannan rana ta zame maki ta farin ciki, shiga kabarin ki ya kasance maki shiga hutun ki, Allah ya sa annabi ya tarbe ki Khairath *Khairath* ki sani ni......... Pagam Humaira ta turo kofar falon nata na biyu tana fadin" wai ya haka Sudais tun da asuba ba zaka bari ka fita a girkin nawa bama ka zo nan ka tare😒 Idannuwanta ta sauke a kan sa, sannan odannuwanta suka sauka a kan abinda ke gaban sa, Ido ta zaro ta murza idannuwanta tabas Sudais ne tsugune gaban gawa da take ganni tamkar Khairath ya yo jina jina tamkar ya tashi a jinya jikinsa du da dan ruwa da ya jika masa suturarsa gefe guda kuma abyar da ya cirw mata ne Ai bata san lokacin da ta dora hannayenta a saman kanta ta kurma ihun da ya sa sudais ya katse abinda ya yi niyar kara fada mata ya mike da sauri dan yin waje da Humaira kar ta daga masa hankali ta kuma bata masa lokacin nan da yake samu na karshe da matar da ta so shi domin Allah daya Ai kuwa kamar ma mai jin tsoron ya taba ta ta juya ta arce a guje tana ihun kuka tana fadin a taimake ta ta yi gefen mahaifan sudais Gaba dayan gidan wannan labari ya girgiza su, a tare suka dugunzuma dakin na khairath banda Humaira da ta yi dakinta tana kuka cike da tsoro ta dauki wayarta ta shiga bugawa dangin ta Dafa kafadarsa mahaifin sa ya yi, shi kansa hawayen ne ya cika masa ido, yana tausayawa dan nasa na cikinsa da yayi muguwar jarumtar nan, ya wanke matarsa da kansa sannan ya zauna yanai mata adu.a Murya a raunane ya ce" ka yi hakuri SUDAIS , ka yi hakuri, ka kara a kan wannan, ka kara yafe mata iyayenta suna hanya ka fito mu je ka sake wannan tufafin mu je mu yiwa matar ka rakiya, Sudais Allah ya jikanta da rahama ba.a so a cika jinkiri da gawa a shinfide Haka ta kasance a wannan rana ta talata, Khairath aka yi mata rakiya gidanta na gaskiya *KULU NAFSIN ZA.IKATUL MAUT* Haka suka dawo aka ci gaba da karbar gaisuwa a gidan SUDAIS UBAN MASU GIDA😟😟😟 RAUDA ce zaune ta buga uban tagumi, wannan abin ya dame ta, yau kwana takwas kennan da take fama sai yau labari ya iso masu cewa matar ogan su SUDAIS ta biyu ce ta rasu domin mataimakinsa yana wajen makokin shi ma sai da Samir ya nemi izinin a fada dan a zo a yi mata adu.a ya bayar da izini ai kuwa nan hankali ya tashi an shirya a gobe za.a je a yi masa ta.aziya motocin ma.aikatar zasu hadu su kai su gaba dayan su an ce a zo karfe goma kowa da kowa Labari na kaiwa Aisha cikinta yayi wani irin juyawa sai kuwa wani kugi ya sa kuuuuuuuuuu wanda ya sa Rauda ta juyo da sauri tana kallon ta, Kafin ta samu damar yi mata tambaya har ta fice a wajen cin abincin cikin gagawa ta tari napep, itama ta biyo bayan ta dan a tunaninta ko bata da lafiya ne Sai dai suna karasowa ta sa kuka mai zafi hannayenta a saman kanta take rusawa Da kyar aka samu ta budi bakin ta ta ce " da matan sa har biyu? To ita wannan ta godewa allah da ta koma tun yanzu Wly ba zan iya raba shi da wata banza ba, ba zan iya ba ba zan iya ba sai na halaka........😳😳😳😳😳😳 *❣IDAN KA RAINA INDA KAKE❣* Na: *SAJIDA* *_LITATAFAN MARUBUCIYAR_* *_Duk Karyar kada_* *_Yar Mahaukaciya_* *_Neman na kaina_* *_Bani da zabi_* *_Daga tafiya daukar soja_* *_Idan ka raina inda make_* *🌈KAINUWA WRITERS✍🏼 ASSOCIATION*🤝🏻 ```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}``` https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation 1⃣8⃣ Tana neman arcewa ya damki hannunta ya ja ta kiiiiiiiiiiiiiiiiii Bai zame ko.ina da ita ba sai bangaren sa, yana zuwa baban falon bangaren sa ya cika hannun ta Tsai ya yi ya dafe goshin sa, zuciyar sa na yi masa duka ta hana shi sukuni sannan ya cika da mamakin kanwar sa Tsoro ne ya kama ta, firgici da tsoron yayan nata ya bayana a tatare da ita, da sauri ta durkusa jikinta na rawa ta ce" yaya, dan Allah ka yafe min, ban shiga wayar ka dan na duba wani abu ba sai dan na tura kati kuma na kali hotunan abaya da Sarkoki, ina cikin kallon ne na ga dossier mai sunna *MATA*, ni a tunanina mata kamar mayayaki irin su abayar ne sai dai ina shiga na ga hotunan nan kamar rayuwarta ce a ciki domin du yawanci wajaje ne da ta yawaita rayuwa a ciki Yaya ka yi hakuri, yauma da na ganta abin ne ya yi surprise dina na tuna ashe ta zo birthday din nan da na so yi maka Dan tsagaitawa ta yi gannin ya tsura mata ido, ai kuwa tsoro ya sa ta saki kuka ta dan kankame hannayenta a jikinta tana dan girgiza kanta tana cike da tsoron sa dan ba zata taba son abinda zai sa ya kai hannunsa kanta ba xan ya taba duka a gaban idannuwanta mutumen ya suma daga marinsa da ya yi Ajiyar zuciya ya sauke gannin Auta kanwarsa wace ya fi kauna cikin yan uwansa yana faman tsorata ta haka bayan bai taba koda shakunarta ba Kansa ya kawar a kalonta ya ja numfashi murya a kausashe ya ce" ki tashi, ba komai zan yi maki ba Da sauri ta mike tana dan kara gyara hijabinta ta matso shi sosai cike da sangarta irin ta autanni ta ce" yayana baka saki fuskarka ba Ya juyar da kansa ya ce" hafsat, tafi Ta kara shagwabe fuska zata yi maganar ya daga mata hannu ya dora dan yatsansa a kan lebensa sannan da dayan hannun ya yi mata nuni da ta tafi Da sauri ta juya ta fice a kasan zuciyarta tana ayana lalai fa wannan lamari mai girma ne, wannan al.amari sai ta saka manya a ciki... Bayan fitarta zama ya yi a saman babar kujerar fallon, waje guda ya tsurawa ido ya jima a hakan yana tunani..., tambayar kansa yake damuwar nan ta kai har ya fara nunawa? Ya san halin kanwarsa ta cika mayar da hankalinta kan abu da nacin abu aman bai taba tunanin zai manta abinda yake ciki ba dan kawai yarinyar nan karama tana kusa da shi! A fili ya furta" ba zaki ci galabar zautar da ni ba *MATA* ! Humaira ce ta shigo da bisimillah, gannin bai amsata ba ya sa ta cire zumbulelen hijabin da ta saka tana sauke ajiyar zuciya dan kuwa yayi mata nauyi ya saka sai gumi take hadawa Kallonsa take a kasan zuciyarta ta shiga furta" ohohoh mutumen nan har yanzu ya kasa sakewa dan kawai wannan rusheshiyar matar tasa ta rasu, to dama mene sauran ciwo kawai ita kulun tana fama ita ba ga kura ba, ita ba turare mai karfi ba, ita ba cin tashi ba, ita ba shan kankara ba, ita ba shan ac ba abubuwa dai da yawa ita sun fi karfinta wannan ai mutuwa hutu ne gareta ma🤦‍♀, ta yatsina fuska ta ci gaba da zancen zucin ta tana fadin sai ka ci gaba da tunane tunanen sai na ga gaban nan wa zakana fakewa da halayensa kanai min gorin na yi koyi da shi domin kuwa Allah ya sa ni din nan dai da ka yawaita nuna bani da halaya ni ce daya kwalin kwal matar naka MU SUDAIS nufarsa ta yi ta dan duka, wanda warin man bleating din da take kamar hauka ya bige shi ya hautsina masa yayan hanji ya saka shi zabura da dawowa a duniyar mutane sannan ya dan ja baya ya sauke mata jajayen idannuwansa a kanta Farfar ta yi da idannuwanta ta kara matso shi sosai ta kashe muryarta ta yi kalar tausayi ta ce" ya dace mijina ya kula da lamarina, kwana takwas fa ba wasa ba Tsai yayi da idannuwansa a kanta, ya kasance namiji mai yawan bukata, yana da yawan kaiwa iyalinsa ziyara sai dai a yanzu ya kasance cikin zulumi, yana afkawa duniyar tunani na irin warin da matar da ta kasance kwalin kwal a wajensa a wannan lokacin da take fitarwa, warin da ba haka take ba ta dai siyawa kanta dan ta birge, wanda yake hana shi nutsuwa maimakun ya samar masa, wanda ke rikita masa dukan wani abin dake tatare da farin cikinsa dan karni ne take tamkar an zuba mata jini a jikinta hakan kuwa koda ta yi wanka da turare ne Katse masa tunaninsa ta yi lokacin da ta dora hannunta na dama saman nasa ta ce" tunanin me kake haka? Har yanzu ba zaka daina tunaninta ba? Ka yi hakuri ka bita da adu.a kar ka shiga hakina Lumshe idannuwansa ya yi bai iya ce mata komai ba, ya mike ya shiga babale boturan rigarsa domin rabun masan nan da ta yi ji yake shi kanshi ya kwashi warin Dakinsa ya nufa yana shiga ya tarar an mayar da katifarsa, an gyara gadonsa an canza zanin gadon da komai harda su turaren wuta Direct bayi ya nufa dan watsa ruwa ya konta ko zai samu bacin da ya jima rabonsa da shi domin kansa har ji yake ya yi masa nauyi sosai Zuzuta kyaunsa, zuzuta kyaun gidan su, na yan uwansa take tunda suka dawo, can ya dora kafa daya kan daya ta ce" mama kin san wani abu kuwa Mamansu ta girgiza kai ta ce" aa sai kin fada Aisha ta ce" matar sa, matar sa, man bleating ne take ya mugun ci mata fata ya shige ta sosai ya bata mata kafa domin kafarta ta shaida ta da hannayen ta, ta wani hakimce ita ga matar gida sai shan kanshi take tana basarwa tamkar ita ce mai kudin, uhum mama zata gane bata da wayo idan na shiga gidan oga SUDAIS, zai ajiye fari na ainahi, kyau na Allah, halita tsarara ba irin nata ba, Mama koda a cikin hijab take ina iya gane yannayin tsarin halitarta ba wata tsarara bace sam wannan ba matar gaban mota bace Mama ta ce" aa, ya akayi du gayun sa ya tsaya a mai bleating? Duk matan nan na duniya? Aisha ta ce" mama, ina tunanin dan na more rayuwana ne Allah ma ya sa ya auri mai bleating Mama zata yi magana wata mata ta yi salama, Cira cira da ita, hijab ne mai ruwan kasa a jikinta aman har ya zama baki dan dauda, ga yaronta ta matkayo shi jikinsa dati har wani shuni yake na dati Gaba daya suka zuba mata ido, ta zube kasa ta shiga gaishe su Mama da Rauda kawai ke amsawa inda Aisha ta yatsina fuska ta tashi ta dauke kofin su na shan ruwa ta mika daki ta dawo tana hade rai tamkar ta ga kashi Matar nan ta ce" dan Allah hajia ki taimaka min ki ban aikin aikatau koda siyen kayan miya ne na ringa yi maki ina samun abinci koda kanzo ne ina ci ina baiwa yarona Ta karasa maganar tana kara risinawa ko Allah zai sa a dace Ido kawai Rauda ta zuba masu, wani tsoron Allah ya kara shigarta a ranta take furta alhamdulilah Allah mun gode maka da ni.imar da ka yi mana , Allah ka kara yi mana arziki mai anfani Muyar mama ce ta katse ta tana kallon matar ta ce" baiwar Allah, da ake zuwa aikatau gidan masu da shi dan ka samu abubuwan anfani na alkhairi ka karu har ma ka kara wasu da shi ke kuwa mai zamu baki a nan? Mu kanmu mun samu na yau muna neman na gobe ne fa Ta kuma sada kanta ta ce" hajia mun yi yawo ne har mun gaji kofa kofa sai dai a kore mu ko a bamu hakuri dan datin nan dake jikin mu, ku yi hakuri ku dauke ni inada kuzari ba zaku yi kuka da ni ba Ke ke ke, malama tashi tashi tashi, mai kike nufi? Da wannan kazantar ta jikin ki da goyo zaki yi wa wa aiki? Kinga mike ki kama gaban ki mu kam ba zamu dauke ki a nan ba! Aisha ta katse ta da mugun fada ranta bace tana nuna kyankyaminta a fili Kara risinawa matar nan ta yi , kana ganninta ka tabata ta jigata, a gajiye take sosai , wahala ta nakasata, ta share gumi ta ce" ki yi hakuri hajiya, yanda Allah ya taimake ki ki taimak........ Ke dAllah malama nace ki mike ko ana dole ne? Ki fice mana a gida tun kafin na wulakanta ki haba! Saurin mikewa ta yi tana kara gyara yaronta da ya tsalara kuka yana kankame jikin mahaifiyarsa cike da tsoron yanda Aisha ke zazaro ido tana masifa tamkar zata doki mamansa Mama bata iya cewa komai ba dan tana gudun furta wani abu ran aishar ya baci hakan ya sa ma ta mike ta yi daki Da sauri Rauda ta fito da leda baka ta bi bayan matar nan da gudu ta ce" malama, malama Dakatawa ta yi ta juyo tana kallon Rauda Rauda ta karaso ta miko mata ledar da naira dari ta ce" ki yi hakuri ki ci gaba da neman aikin, Insha Allahu zaki dace, ga wannan tufafina ne duda sun sha ruwa ki samu ki canza naki sai wannan kadan ne ba yawa nima iya shi ne ya rage min Allah ya sa ki samu aikin Godiya ta yi ta yiwa Rauda inda ta tsaya ta bita da kallo har ta shige gidan su Murmushi ta saki ta bi kudin da Tufafin da kallo a fili ta furta" *alkhairin ki zai bi ki RAUDA* (😳😳😳😳😳) *❣IDAN KA RAINA INDA KAKE❣* Na: *SAJIDA* *_LITATAFAN MARUBUCIYAR_* *_Duk Karyar kada_* *_Yar Mahaukaciya_* *_Neman na kaina_* *_Bani da zabi_* *_Daga tafiya daukar soja_* *_Idan ka raina inda make_* *🌈KAINUWA WRITERS✍🏼 ASSOCIATION*🤝🏻 ```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}``` https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation 1⃣9⃣ Matarnan na gama fadar hakan ta fice! Rauda na komawa ta tarar aisha sai fada take tamkar ta ari baki, tana rantsuwar idan ta Auri Sudais ba zata dauki yan aiki a nigeria ba dan kuwa ba zata amince tana ji tana gani a kawo mata karnin talauci ba! Rauda ta girgiza kai kawai ta shige bayi dan dauro alwallah Har karfe tara na safiyar larabar nan Rauda bata fito daga dakinta ba, hakan ya sa mahaifiyarta shiga tana fadin" RAUDA, lafiyarki kuwa na ga har kin yi lati yau bayan nan da kwana hudu za.ai maku albashi kar ki yi wasa fa a taba maki albashin ki Rauda dake konce saman katifar su tana ta bari, jikinta ya dume da mugun zafi ta kasa furtawa mamanta komai dan kuwa bata jin zata iya buda bakin nata Da sauri Nana Mariama ta karasa tana fadin" subahannalahi, Rauda da zazabi kika tashi yau? Ya Allah ka ji kaina kar ta yi maki irin abinda take maki Idan rauda na zazabi takan yi mata duka ne mai zafin gaske domin har combilser take tana zabura jikinta na dumewa da mugun zafi har rike su ake a asibiti , zazabi dai bayai mara da dadi Janye rufar da ta yi da hijabi ta yi, ta dora hannunta a saman wuyanta, da sauri ta janye hannun tana fadin ta faru ta kare domin kuwa jikin Rauda har wani huci yake saki kuma da alama bama ta gane wanda ke kanta ta fara yin nisa Jiki a sanyaye ta konce harshen zaninta, daman da dari uku ta tashi, mahaifin su Rauda ya kara mata dari hudu kafin ya fita, Aisha ta karbi dari hudun ta bara mata ukun wanda ta yi niyar ta baiwa Rauda dari biyu ita kuwa ta sha garin kwaki da rana Ajiyar zuciya ta saki domin kiwa dari ukun nan ko kudin mota ba zai ishe su zuwa asibitin gwanati ba bale a yi maganar siyan magungunna dan kuwa koda an duba ka kyauta kai zaka sayi maganinka Mayar da dubanta ta yi wajen Rauda, dan haka ta mike da gagawa ta janyo hijabinta ta kara dakin na rauda ta fita da mugun sauri ta tari mai napep ta dawo ta talaba da kyar ta saka mata hijab ta fito da ita ta rufe gidan suka shiga adidaitan ta yi masa kwatancen gidan yar uwarta ko Allah zai sa ta bata wani abin ta kai Rauda asibiti Suna zuwa ta fito da rauda ta bashi dari biyu da hamsin yayi mata sauran naira hamsin ta talaba Rauda ta shiga gidan bayan ta gaisar da mai gadi ta gaisar da kishiyar yayar tata wace ta amsata a yatsine tana nuna kyankyaminta a fili Tana shiga baban falon Yayar tata ta samu ta shinfidar da Rauda saman doguwar kujera saman wani dan kwali ne ko hula ita kam bata tsaya lura ba Mai aikin Aunty salma ce ta shiga dan sanar da ita zuwan kanwarta NANA MARIAMA AUNTY salmar ce ta fara fitowa da fara.a a fuskarta ta zauna suna gaisawa nan ta lura da Rauda ta ce" kai wannan kamar mai kin gidanna ( haka take kiran Rauda, domin sam Rauda bata son zuwa gidanta dan yarinyarta Sarah dake da wani irin hali irin na mahaifinta wulakanta talaka koda kuwa dan uwanta ne) Murmushi Mama ta yi ta ce" eh ita ce, zazabin nan nata ne ya zubo mata, mu kuwa mun tashi garin a cure Auntu salma ta fahimci inda zancen Mama ya nufa, ta sauke ajiyar zuciya ta dafe kanta, murya a bace ta ce" kinga irinta ko Mariam, kin ga abinda nake fada maki ko? Ki duba ki ga irin rayuwar da kika zabarwa kanki , ke soyaya ko? Ki duba ki ga da kyanki, da dirinki kika kare a talaka wanda shi kansa bai samu cin yau bare na gobe ba harda su haihuwa da shi dan kasada, ke yanzu da ban sa an tsayar da haihuwar nan taki ba fa da kin ci gaba da zubo masa yaya yana takama ya ajiye zudediyar mata a gida bayan ya kasa magance maki matsalolin ki bare na yayanki, yanzu wannan abin kunyar har ina? Yarinya karama da ke aman du wahala ta saka kin yamutse tamkar kece babar ni kuwa kanwarki,? Rauda ce ta fara sakin dan nishi a hankali ta shiga dan mimikewa tana juya kanta a hankali wanda ke nuni da tana jin jiki sosai Ido ta dan zaro ta ce" wai kwannan duniya dama haka zazabi ke wahalar da ita? Kuma kin tabata ba wani ciwon ke dawainiya da ita ba? Mama ta sauke ajiyar zuciya bayan ta bi Rauda da kallo, ita tama kasa magana sai gyadawa yayarta kai kawai da ta yi Sunnan Sarah ta kwala da kira wace ta fito da waya tana ta zuba sangarta tamkar yarinyar goye ta mikawa mamanta waya tana fadin" Mom kin ga grandma ko? Wai dole sai na je birthday din limo ni dai aa ba zan tafi ba Ido Mariama ta zubawa Auntynta wace ta karbi wayar mahaifiyarsu tana dariya tana amsa kiran , ji take tamkar ta karbi wayar ta zube a kasa ta bata hakuri, ta fada mata ta yi nadamar bijire masu da ta yi , ta fada masu su yafe mata su karbeta da yayanta Tana ji tana ganni har ta gama wayar ta kashe sannan ta yiwa Sarah umarnin ta dauko mata dubu goma a cikin jakarta Sarah ta yatsina fuska, ta bi kanwar mamarta da kallo mai shigen harara bata iya ta gaisar da ita ba ta juya a kasan zuciyarta tana furta sai na fadawa grandma ko matar nan mai nacin tsiya zata bar mu mu sarara a cikin gidan ubana! Tana fitowa ta mikawa mamanta kudin ita kuwa ta baiwa Mariama ta mike tana godiya ranta a mugun jagule ta cicibi Rauda ta talafota ita kadai suna kallonta har ta fice a fallon Da kyar ta samu mai napep ta tsayar ya dauko su ya kai su asibitin gwamnati Yelemin kuwa suna zuwa aka basu gado aka rubuta magungunna ta tafi nema wanda tashin farko sai da ta kashe dubu biyu ta dawo ta mikawa likitocin nan aka yi mata allura aka saka mata karin ruwa Yau kwannan Rauda biyu a rike a asibiti, sai dai sam bata dayo yanda ake so ba A yau ne Sudais ya diro kampani dan gyara takardun biyan ma.aikatansa Tunda ya zo yake zuba ido dan gannin ta inda zata fito, aman shiru ba ita ba alamarta har lokacin cin abinci ya yi Salif ya kawo masa nasa ya juya aman ya kasa koda kallon abincin ne bare ya sa ran zai iya ci, a hankali ya dana wayarsa ya shiga laluben lambar SAMIR Salif na fitowa ya dubi kofar Rauda, shi kam ya rasa ya zai yi da tunaninta, ta zo ta tsaye masa a zuciya ta hana shi sukuni aman yau zai bi yayarta ko zata fada masa inda take ( kai ko😳) Tunda ta fito yake dan binta da motarsa 4×4 aman ta ki tsayawa Gannin ba zata tsaya ba ya saka shi fitowa da sauri ya sha gabanta ya hade hannayensa biyu ya ce" Auntynmu dan Allah ki saurare ni, ki yi hakuri aunynmu na kasa jurewa ne kwana biyu bata zo aiki ba, ina cike da zulunmin ko ta fasa aikin a nan ne, Aunty ina Rauda ta shiga kwana biyu? Ja ta yi ta tsaya, cikin yan sakwani ta karanci Salif, ba laifi gy din ya hadu sannan da yan canjinsa ta yi murmushi a ranta take ayanna wace rana Rauda ta yi abin kanta, dan kuwa Salif bashi da laifi Dan yatsina fuska ta yi ta ce" menene tsakaninka da kanwata? Salif ya dan sosa keyarsa ya kallo Aisha ya ce" auntynmu ina fatan dai ba.ai mata miji ba? Aisha ta dan saki murmushi ta girgiza kanta ta ce" eyah, LALLANA bata da lafiya ne tana asibiti ma an kama ta Ido ya zaro harda dora hannun a kansa ya shagwabe fuska ya ce" eyah, rashin lafiya bai yi min adalci ba, aman aunty ya za.a yi na ganta ne? Aisha ta kara waigawa ta kali motar, kalar ruwan baki ce, a ranta ta ayanna ba laifi zan dan kankaro mutunci , ta ce" ai yanzu ma can na nufa idan kuwa zaka je mu tafi Samir dake nesa da su bai san mai suke tataunawa ba, shi dai yana biye da ita ne bisa umarnin ogansa dan sannin inda Rauda ta shige kwana biyu wanda da kyar ya kwaci kansa bisa uzuri da ya nema ogansa ya yi masa Gani ya yi Aisha ta shige motar Salif, ya girgiza kansa a fili ya furta ke kam sai kace taxi? Kowa ma so kike! Biye yake da su har suka karaso wajen asibiti inda Salif ya tsaya wajen masu abarba da lemo da sauransu ya sayi kaya guda ya biya suka shiga A hankali Samir ya tsayar da motarsa ya fito ya bi bayansu A cikin dakin mutun biyar ne a konce, kowane da masu jinyarsa abinka da ba mutun daya ko biyu ba sai dakin ya dume yake fitar da wari wari hakan kuwa du iya kokarin mama wajen kuna turaren haki da ya cinye sai warin ya dawo Suna shiga Aisha ta ja dankwalinta ta rufe hancinta ta nufi wajen gadon tana yiwa Salif iso Har kasa ya duka ya gaishe da Mama mariama, shi kuwa Samir ya ja kusan wani tsoho marar lafiya da yake barci ya tsaya yana sauraron su Aisha cike da fara.a ta ce" mama, wannan saurayin Rauda ne a wajen aikin mu yake shi ne gaba daya chef din bangaren abinci Wata irin bugawa kirjin Samir yayi , jin abinda ake fada , Salif.... ne saurayin Raudar?????? Katse masa tunani suka yi lokacin da Salif ya dawo da docter yana fadin" docter, a taimaka a bamu patient dinmu mu koma privet hospital Dumdumdum gaban Samir ya kuma faduwa, ya rasa hanawa zai yi, kallo zai yi har su gama? Ko ya zai yi? Shi dai abinda yake da tabacinsa shine ba Salif kadai ba shi kansa a matsala yake....... *❣IDAN KA RAINA INDA KAKE❣* Na: *SAJIDA* *_LITATAFAN MARUBUCIYAR_* *_Duk Karyar kada_* *_Yar Mahaukaciya_* *_Neman na kaina_* *_Bani da zabi_* *_Daga tafiya daukar soja_* *_Idan ka raina inda make_* *🌈KAINUWA WRITERS✍🏼 ASSOCIATION*🤝🏻 ```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}``` https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation 2⃣0⃣ Bai gama yanke hukuncin abinda ya dace ya yi ba ya ga nurse biyu sun tura RAUDA saman garon asibiti mai taya an shige ambulance da ita su kuwa su Salif sun shiga motar sa da Mama da Aisha Hannayensa biyu ya dora saman kansa a fili ya furta" na shiga uku! Daidai lokacin wayarsa ta kwashi kuka, da sauri ya daukota a aljihunsa ya duba sunnan mai kiran *OGA SUDAIS* ya gani a rubuce hakan yayi daidai da bugawar zuciyar sa Kin dagawa ya yi ya nufi motarsa ya tada ya bi bayan su a guje wanda da kyar ya samu ya cin masu suka karasa asibitin tare Karban su aka yi da hannu bibiyu aka basu gado , nan kwararun likitoci suka shiga aikin su kan Rauda Jiki a sabule Samir ya juya ya nufi gida wajen Sudais...... Aba na zuwa asibitin gwanati ya ga wayam ba su Raud ba alamunsu gadon da take har an dora wani tsoho Gabansa ne ya yanke ya fadi, shi dai da safe kafin ya tafi Nema a yanda ya barta bata ma shaida wanda ke kanta domin jikinta zafi rau ta zubo mata kuma yanzu ya dawo ya ga basa nan Da mugun sauri ya juya ya nufi wajen likitocin, tun kafin ya karaso yake yi masu nuni yana tambayar su inna yarinyarsa? Da yake wasu likitocin ne suka canji wa.incan sai suka tsaya sokoko dan kuwa basu san wace yarinyar tasa ba! Abinka da halayen wasu likitocin har sun fara yi masa masifa , daya daga cikin wanxen nurse din ta fito ta gan shi nan ta fada masa ai sun canza asibiti sun koma ta kudi ta fada masa sunnan asibitin Tsai ya yi ya dan jima kafin yake samu ya fita a asibitin Tafe yake yana tunani a cikin zuciyarsa, tambayar kansa yake wai dama idan *baka da kudi ba.a gannin mutuncin ka? Maganarka ma zaka rasa mai saurare?* yanzu ya dace abinda Mariam ta yi masa kennan? Koda bashi da karfi, koda ba lalai ne ya bada gudunmuwarsa a haka ba koda aljihunsa ba nauyi yana da iko na matsayin da Allah ya bashi na mahaifin yaran nan, aman komai ta tashi sai ta shige gaba ta aikata abinta ba ruwanta da ya zai ji, mai zai ji, bale a kai ga abinda yake so a yi ko kar a yi wato umarninsa ko ra.ayinsa! Yakan tambayi kansa shin rabuwarsa da uwar yayansa ne ya fi masa alkhairi bayan tsayin shekarun nan ko hakuri zai yi ya ci gaba da fuskantar matsaloli irin haka kamar yanda aminina Salisu ya sha fada min Allah jikan rai cewa *Ahmad Auren yar masu kudi kai talaka gaba da baya,? Ahmad kana son ka saka kanka a tashin hankali ne ko me? Menene damuwarka da zaka kai kanka ka saka a irin wannan rayuwar a matsayinka na wanda aka ajiye ba baka ba wani ajiya ba? Dadaya ne a cikin irin yayan masu kudin nan zaka aure su ku zauna lafiya kai ko mai kudi dan uwansu sai ka zamto a sama kake kaima! Ka kara tunani kar ka dawo ka ringa dana sani daga baya* Ajiyar zuciya ya sauke ta barkatai a fili ya furta" ba laifina bane aminina , giyar soyaya da tausayin Mariama ne suka kwashe ni idannuwana suka rufe ta yaudare ni sa kalamanta da nuna tsantsar soyayarta wa ni ta dawo yanzu take wulakanta ni, Ya Allah ka yi min magannin wannan damuwar ya ubangiji Glas na inox ne ya saki ya fadi kasa tartsatsa cike da tashin hankali ya juyo ya ce" bata da lafiya? Tun yaushe? Me ke damunta? Kuma a ina take? Wani likita ke kulawa da ita ne? Samir ya ce" oga ai a asibitin gwamnati take, yanzu salif ya mayar da ita ta kudi Tsai yayi ya dakata jin suna salif, wai salif waye kuma salif? Tsare Samir ya yi da ido, yana jiran jin karin bayani aman shiru samir sai wani kara sada kai yake tamkar yana gaban sarki Sudais ya ce" a tunanina bata da dan uwa muharaminta mai suna SALIF! WAYE SALIF! Ya karasa yana daga murya Samir ya dan ja baya ya shiga koro masa dukan abinda ya faru a gaban idannuwansa Sudais kai tsai yayi tamkar gunki yana sauraron abinda Samir yake fada, wai wani gardi, gardin ma Salif, yaron da ko gaishe shi zai yi sai ya risina yana girmama shi yana kiran shi da yayan sa, yaron da idan fito na fito ne ba zai yi gigin ya dora sahunsa a kan na Sudais ba shi ne yake son *MATA!* juyowa ya yi ya ce" du yanda aka yi laifinta ne, laifin yarinyar nan ne, dan me ita du inda take sai ta yi kokarin tayar min da hankali ta ja min bacin rai? Wai me ke damunta ne haka? Yanzu a shiga wajen cin abincin har ta yi sabon da ta kula soyaya da wannan karamin yaron? Ya hade hannayensa ya jimke ya ce" Ni kuwa karya suke gaba dayan su, ba zai yiwu na yi takara da wannan yaron wajen neman soyayar Mata ba! Ko ya ki ko ya so, ko mutuwa take itama sai ta barshi! Samir menene aibuna da yarinyar nan ta kasa fadawa tarkon so na kamar yanda sauran yan matan ke so na? Ko dai ita ganina take tamkar dodo? Ya karasa yana tsare samir da ido Samir ya sauke ajiyar zuciya, domin a yanda ya tsamaci abin ya zo masa da sauki, aman abinda yake tsoron fada a yanzu shine abinda yake son fadawa ogan nasa Samir ya dan kara gyara zaman sa ya ce" Elhaj ni da san samu na yi da na fada maka salon yan matan zamani masu aji Sudais ya dan dage girarsa ta dama ya kara tsare Samir da kallo Samie ya ci gaba da magana gannin bai kyare shi ba ko ya dakatar da shi, ya ce" wato oga, yan mata fa sunna suka tara, wasu zaka ga dan tsabar zubar da aji su da kansu zasu fadawa namijin suna son sa, wasun kuwa cikin dabara zasu karlato da hankalin saurayin, wasun kuwa koda soyayar namijin nan zai kashe su ba zasu taba amincewa su sanar masa ba da jan aji da gudun kar namijin ya raina su Sudais ya zauna da kyau kamar da gaske dauka yake ya ce" to ai ni ba zan rainata ba dan ta furtan kalmar so, ainahi ma shine abinda nake zaman jira a nigeria Samir Samir ya yi tsam, ya kare yiwa ogan nasa kallo, a ransa yake fadin lale oga bashi da ranar barin kasar nan, Samir ya ce" aa oga ai kai ya dace ka tunkare ta, ka nuna mata alamar soyaya, ka furta mata kalaman so hakan zai sa ta karbe ka kila wa kala Sudais ya yi murmushin da bai kai zuci ba ya ce" ya ake yi kennan? Samir ya dago galala yana kalon sa, wai yanzu yana nufin bai taba yin haka wa matansa ba? Aman dan gaskatawa ya ce" ai oga yanda kake nunawa Su Gajia Sudais ya girgiza kansa, ba zai iya furtawa Wani sirrin dake tsakaninsa da matansa ba, ba zai fadi hakan ba, dan haka ya kuma sakin murmushi ya ce" kana dai nufin na shirya, na yi wanka na je kofar gidan su na aika yaro kiranta, idan na ci sa.a ta fito sai na isar mata da sakon zuciyata cikin lalami da roko ko? Samir ya saki murmushi ya ce" haka nake nufi oga, ka lalabata ka bita zaka ga an dace Sudais yayi yar dariyar da rabonsa da ita har ya manta, ya tafa hannayen sa biyu ya nuno samir ya ce" SAMIR ai ban san cewa tare da dakiki nake zaune shekara da shekaru ba sai yau! Samir ka tabata karatun sa ka yi ba.a yi maka taimako irin na yayan manya ba? Ina da ja a kararun ka sannan ina da ja a hankalin ka, Kai yanzu yarinyar mai shekara 22 a duniya ce zan je godai godai da ni na hade hannaye ina neman soyayar ta? Karya take, kaima karya kake Samir, sannan du wani banzan da zai nufeta karya yake! *RAUDA'S MINE* kuma zata nemo SUDAIS dinta da kanta! Samir galala ya yo tamkar sakarai, wai ashe du sauraron nan nasa da oga ya yi dan ya auna girman shirmen sa ne? Ya salam! Sudais ya kakausa muryarsa ya ce" abinda nake so da kai ka tashi ka kai ni asibitin na canza mata waje na kaita clinik! Yana gama fada ya mike ya fice inda Samir ya biyo bayansa da sasarfa a kasan ransa yana tambayar kansa ta yaya kennan hakan zata faru??? 👏🏻😊👏🏻 *❣IDAN KA RAINA INDA KAKE❣* Na: *SAJIDA* *_LITATAFAN MARUBUCIYAR_* *_Duk Karyar kada_* *_Yar Mahaukaciya_* *_Neman na kaina_* *_Bani da zabi_* *_Daga tafiya daukar soja_* *_Idan ka raina inda make_* *🌈KAINUWA WRITERS✍🏼 ASSOCIATION*🤝🏻 ```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}``` https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation 2⃣1⃣ Suna karasowa ya bi assibitin da kallo, ya girgiza kansa a ganninsa a irin albashin Salif ya kare a wannan asibitin? Sauka ya yi daidai ana kiran salar magariba, kuma asibitin ta fi kusanci da gidan su Rauda domin ta kudi ce kuma a wajensu take Buta ya dauka ya yi alwallah kamar yanda duban bayi suka yi suka shige masalaci dan gabatar da salar magarib Suna gamawa yawancin jama.a suka fito inda da yawa suka zauna sai sun yi ta isha.i suke fitowa ciki kuwa harda Sudais da samir A hankali samir ya dan matso Sudais na jan carbinsa fari kal ya nutsu Samir ya ce" oga ga mahaifin Rauda zai fita Bai katse adu.arsa ba, bai dago kansa ba ya ci gaba da adu.a yana neman karin kusancinsa da ubangiji Malan Ahmad ya matsa sosai kusan limamin masalacin ya duka ya sada kansa murya a raunane ya ce" Allah ya kara yawan Rai ina son dan tataunawa yanzu, a yi min afuwa na tabata yanzu daidai lokacin karatu ne aman ina tsoron a gama salah jama.a su watse ni kuwa ina da ciwo a zuciyata Gama sauraronsa liman ya yi, ya kai aya ya ajiye alkur.anin dake hannunda ya ce" malan Ahmad mai ke faruwa haka? Na tabata baban abu ne Malan Ahmad ya kuma sada kansa, ya shiga dan fadawa Liman kadan daga cikin abinda yake ciki na iko da matarsa take masa kan yayansa, ya gabatar masa da hujoji ya tunawa liman shi kansa ya taba yi masa fadan ya aka yi bai yiwa yayansa aure ba da an zo neman auren matarsa ta kori mutun baya tsoron sharin mutanen zamani? Lima ya gyada kai yana sauraron sa Ya ci gaba da fadin" yarinyar wajena wace du idan ana sauka nakan sakata a adu.ar Allah ya yaye mata irin zafin zazabin dake damunta ya yi mana dalilin da zamu hadu da maganin abin ce ciwon ya tashi Liman ya ce asha asha subahannalah fatan da sauki Malan Ahmad ya kuma sada kansa yana hangen agogon masalacin ya ga da saura lokacin sallar isha.i dan haka ya ci gaba da fadin" Alhamdulilah a zuwan da na yi dazu da yama tana zaune har ta ci abinci, Liman Wato rashin lafiyar nan da ta yi wannan karon da farko abinda ya girgiza min zuciya wai na zo asibiti na tarar da Mahaifiyar tata ta canza mata asibiti Ina zuwa na tarar an bata daki, kayan ciye ciye da shaye shaye a zuba kai dai abubuwan sun kai jarin wani mai karamin karfin To da yake na tarar da yayarta ta zo ganninta sai na yi tunanin ko ita ta kawo? Dan haka da nuna fara.a na shiga godiya wa yayar tata na ce Sai dai ban gama godiyar ba ta katseni da yannayi na matan da suka so su fi karfin mazajen su tana fadin" ai saurayinta ne ya kawo , ainahi ma saurayinta ne ya canza mata asibiti daga ta talakawa zuwa ta masu kudi, Aka nuna min saurayin yana zaune ya hakimce bai yi tunanin ni mahaifin yarinyar bane aman a tunanina da yana da da.a koda ba kowa bane ni datijo ne Mahaifiyarta ta ci gaba da fadin" ai kam Rauda ta yi ba zata, ana tunanin ta yi bakin jini ne ashe ita da wanda ke sonta zamu warke da talauci, ka duba ka ga Malan wannan sayaya duka a lokaci guda Yar uwar tata ta furta" wannan ai ba komai bane, kema lokacin da kike soyaya da Elhaj brah ai kin ga, kaf cikin gidanmu har yanzu kece aka fara baiwa mota kafin auren ki aman kika bige da aurwn soyaya yanzu kike cin soyaya Malan irin haka na faruwa a kulun kwannan duniya, abinnan na ci min tuwo a kwarya na hana ni sukuni Yanzu so take Raudar ma daje tausaya min ta juye mata tunani domin yau da gobe sai Allah Liman ya ci gaba da girgiza kansa, yana al.ajabin halayan wasu matan, a gaskiya a irin samun Malan Ahmad yana matukar kokari da iyalinsa aman rainuwa da raina inda ya ajiye su ya saka a kulun bakin alkhairinsa matarsa ke gani har yarsa baba ta tashi itama da halayen karamar itace ya isa da ita, gashi itama ana kokarin cusa mata wani ra.ayin! Murya a rausashe Liman ya ce" ka yi hakuri Malan Ahmad, ka kara hakuri, nima ka kara yafe min, domin da farko na yarda da abinda aka zo aka fada min cewar ka sakawa yaya ido suna abinda suke so da matarka a anguwa, sai daga baya na fahimci matsalar, ka kara hakuri malan Ahmad ka daina sakawa a ranka ka ci gaba da rokon Allah ya shirye ta ya shiryi iyalinka baki daya, domin yanzu wasu matan kwadayi na rufe masu idannuwan su har su ringa aikata abubuwa tamkar zararu Malan Ahmad ya yi murmushi ya ce" liman da na nuna bacin raina, *MARIAMA* ni ta kali kwayar idannuwana a gaban yayana, da yayarta, da yaron da take tunanin watarana ya zama sirikina ta furtan kalamai kamar haka" MALAN wai me ke damunka haka? Kana yiwa iyalinka bakin ciki kiri kiri, zamu canza kalar miyar mu kana jin haushi sai dai mu dawama da tsanwar miya da dadawa da gari ko? To Malan Ahmad baka isa ba, ba abinda ka isa ka yi da wannan lamari kuma, Rauda kamar ta auri Salif ta gama dan ba zan yarda da raina da lafiyata ka nakasa min yarinya kamar yanda ka nakasa ni ba! Malan in takaita maka a gaban bayin Allahn nan ta rufe ido ta yin fata fata ta gama ikirarin ba abinda na isa na yi a rayuwar Rauda, Liman Yar cikina Ya karasa yana sada kansa kasa Liman ya kuma jujuya kansa yana dan waige kar a je wasu na ji, inda Sudais kansa ke sade yana jan carbinsa aman gaba daya abinda Wannan bawan Allahn dake kokarin tarwatsa masa kwakwaluwa na dukan cikin kunnansa domin Allah ya yi masa ji a kasan zuciyarsa har ya tsayar da adu.ar jan carbin kawai yake, kokowa yake da kunnensa aman fafur ya ki bashi damar sarafa shi, ya biyewa umarnin zuciyarsa cewa sai fa ya ji karshen maganar domin magana ce da ta shafi *MATA* a kasan zuciyarsa yake maimaita" innalilahi wa.ina ilaihi raj.une, Mata bata samu tarbiya mai kyau ba? Me ke shirin faruwa da rayuwana ne? Shin soyaya zata rufe min ido na auri mata na kawo ta gidana koda kuwa babu rabon haihuwa tsakanina da ita ai tana iya bata min zuri.a, Kara sada kansa yayi ya ci gaba da sauraron magangannun malan Ahmad domin kowa ma jinsa yake dan kuwa bai sirinta muryarsa sosai ba Liman ya ce" subannalah, subannalah, abu bai yi dadi ba, Allah ya shirya, Allah ya shiryar mana zuri.ar mu baki daya Malan Ahmad mahaifin su Rausa ya sauke ajiyar zuciya ya ce" liman ai aikin gama ya gama, domin a yau a yanzu a masalacin nan bana so na fita ba tare da ka daurawa yayana aure ba! A yau zan nunawa Mariam da ahalinta na isa sa yayana, Liman du mai son RAUDA ko AISHA ya fito na karbi sadakinsu da salatin annabi sallalahu alihi wa salam a daura aurensu a yau yau din nan Dum dum dum gabansa ya fadi, da mugun sauri ya dago da kansa daidai lokacin Ladan ya dauki lasifika ya kwala kiran salar isha.i To readers, cmment fa ko na tafka tsiyar😊😊😊😊😊😊🤣🤣🤣🤣🤣 Shin yaya Sudais zai yo da wannan cakwakiya? Yau satin matarsa biyu da kwana hudu da rasuwa, a al.adarmu ta hausa shin zai amince da wani tsari daban,? Zai ci gaba kuwa da sonta bayan a jin da yayi RAUDARMA bata da tarbiya! Yaya za.a kare da wannan cakwakiya *AISHA KO RAUDA WACECE MAI RABON?* *❣IDAN KA RAINA INDA KAKE❣* Na: *SAJIDA* *_LITATAFAN MARUBUCIYAR_* *_Duk Karyar kada_* *_Yar Mahaukaciya_* *_Neman na kaina_* *_Bani da zabi_* *_Daga tafiya daukar soja_* *_Idan ka raina inda make_* *🌈KAINUWA WRITERS✍🏼 ASSOCIATION*🤝🏻 ```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}``` https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation 2⃣3⃣ *YA ALLAH KA HANE MU SHIGA HAKKIN BAYINKA KA TSARE MU FADAWA HALAKA KA YAFE MANA KURAKURAN MU KA SAKA MU CIKIN BAYINKA MASU YARDARKA KA TSARE MU JIN KUNYAR LAHIRA DA TA DUNIYA AMEN AMEN* Dady bai dauki wani dogon lokaci ba abinka da dare ba wani go slow sosai domin du jama.a sun yi gida tsiraku ne ke yawonsu a cikin gari Gaisawa suka yi da jama.ar wajen cikin mutunci wanda sai a nan Sudais ya gabatar masu da kansa da kuma mahaifin sa A hade ya baiwa dady labarin ko su su waye domin marigayi uban marayu sanane a garin dan ya yi sunna sannan har ya koma ga mahalicinsa ba.a yi masa muguwar shaida ba Sudais ya mike ya cewa mahaifinsa yana son maganar sirri Gefe suka koma, Sudais ya sada kansa kasa, muryarsa ya raunana ya ce" Dady, kana tune da alkawarin da ka taba yi min a ranar da kuka sanar da ni kun zaba min matan aure biyu aman hakan ba zai hana ku tauye min hakina ba idan na samu mace ko yar gidan waye zaka shige min gaba ka aura min? Dady ya ce" kwarai kuwa Son, ba zan manta alkawarin da na daukarwa kaina ba Sudais ya sauke nanauyar ajiyar zuciya ya kali dady ya ce" dady sai dai ina cike da tsoro, na hadu da yarinyar nan a wajen danja, tun daga ranar dady nake adu.a idan alkhairina ce Allah ya tabatar min idan kuwa ba rabona bace ba alkhairina bace Allah ya nisanta ni da ita Dady a kulun sai ya zamto kusancina da ita kara karuwa yake aman ita bata san bama abinda nake ciki ( ya boye mata abinda Aisha ke ciki) ya ci gaba da fadin" a yauma zuwa na yi dan dubata ba lafiya zazabi sai kawai na riski wannan lamari...........ya kwashe du yanda aka yi ya fadawa dadinsa domin Sudais bashi da tamkar dady sannan ya tabata abinda zai hango masa shi bai isa ya hango shi ba ko dan ya kasance shi daya cilo ne dansa namiji suna sa kyakyawan fahimta a tsakanninsu suna fadawa juna sirikansu suna rufawa junnan su asiri tamkar wasu aminan juna Dady kansa ya jinjina abin a cikin ransa, sai dai abubuwa da dama sun daure shi sun hana shi yin gardama wa abin du da irin tarin abubuwan da basu yi masa ba a tatare da yarinyar duba da halayen da mahaifiyarta ke da, da rashin sannin takamaiman itama halayen nata irin hakan ne ko kuwa ? Ga mutuwar Khairath sati uku da kwana hudu ko adu.ar arba.in ba.a yi ba da dai sauran su, aman kuma idan ya yi duba da adinnin musulunci bai hana irin hakan ba, sannan ya tabata sudais ba zai yi masa karya ba, ga girman alkawarin da ya daukarwa dan nasa Dan haka kunayensu zasu toshe a daura auren sai dai zai nemi alfarma idan har iyayen sun amince tarewar a basu koda sati uku ne a yi adu.ar kwana arba.in din Khairath Karin shaidu aka samu , cikin ikon Allah aka daura aure, a baban masalacin juma.a, a daren alhamis karfe goma saura bisa mafi darajar sadaki aka gama da karatu aka rufe aka fito Tunda ya fito suka yo salama da dady kan sai sun hadu a gida ya nufi asibitin Samir na biye da shi a baya yana kallon sa mamakinsa bai gama gushewa a fuskarsa ba, yana mamakin Sudais a tunaninsa zai janye ne zai fasa maganar sonta idan ka yi la.akari da halayen sa na kyamatan yan mata masu baudadan halaya aman ya aure ta ba tare da dar ba Saurin da yake ne ya sa shima ya daga kafarsa ya fada masa sunnan room din wanda sun kusa karasawa su Salif sun fito da aunty da yarta sarah ta rike hannunsa gabjejiya da ita haka kawai dan ta ga mai dan hannu da shuni har suna ta yi masa da mijin mu😊 Saurin sakatawa ya yi gannin ogansa sannan ya janye hannunsa a rikon da ta yi masa ya yi gagawar zuwa yana dan risinawa yana gaisar da Sudais Kallonsa kawai yake, sai yanzu ma ya fito daga wajen su kennan? Aman ita fa wannan da yake rike da hannunta kanwarsa ce? Bai iya amsa shi ba ya yi office din docter inda Salif ya bi Samir da tambayoyin wani ne ba lafiya ba Samir ya yi masa kalon tausayi kake bani ya girgiza masa kai ya juya shima ya tsaya dan jiran fitowar Sudais Sudais ya dauki lokaci a wajen docter kafin yake fitowa Bai ko kali inda dakinta yake ba ya umarci Samir da su tafi Samir kam bai iya yi masa tambayar komai ba shima ya ja bakinsa ya yi shiru dan baya son abinda zai jaza masa matsala da daren nan Da safe Docter ya shigo masu da salama ya fada masu cewa Elhaj ya umarta da a ringa zuwa gida ana duba ta Mamaki ne ya cika Mama dan kuwa ita a tunaninta du Salif ne ya yi wannan kokarin , ta jinjina kanta cike da murna suka shiga harhada kayan su tana fatan Salif ya zo ta yi masa godiya Rauda kam abin ya girmami tunaninta , ita tambayar kanta ma take a ina suka fara soyaya da wannan mutumin da har ya baiwa kansa damar yi mata wanbab hidindimun? Tana fatan ta koma bakin aikinta ta biya shi dukan kudaden da ya kashe mata dan kuwa ba zata amince kudin saurayi ba dan gudun gobe ya fito mata ta wata hanyar Mama ta kale ta ta ce" haba Lallana (ta dawo kiranta da lalla tunda ta ga kudi🤦‍♀) shin mai ke damun ki ko bakya so ne mu tafi gida asibitin bai ishe ki ba? Ai ko dan albashin ku ma koma ku je ku karbo ko? Rauda ta juyar da kanta tana saka hijabinta Aisha ta yatsina fuska bata ce komai ba Direba ne a kofa a tsaye suna fitowa ya gaishe su ya ce" Elhaji ne ya turo ni na mayar da ku gida Da mamaki Aisha ke kallon sa, Elhaj kuma? Dama salif haka yake da yayan banki? Aa wannan lamari da dadi yake Ai kuwa ita ce gaba gaba ta hakimce su Rauda a baya direban ya ja su ba tare da sun zurfafa tunani ba ya kai su har kofar gidan su ba tare da sun yi masa kwatance ba kuma basu yi mamaki ba domin dai salif ba sannin gidansu yayi ba Malan Ahmad ne zaune saman darduma kasan shukar maina dake cikin gidan da carbi a hannunsa yana ja Suna shigowa su suka yi daki dan kai kayan su ita kuwa ta nufi inda yake zaune direct ta durkusa har kasa kanta a kas ta shiga gaishe shi Ido ya tsura mata, tsoro yake har cikin ransa kar a je itama ta koma irin su, hakan ya sa ya kasa buda baki ya amsa mata gaisuwarta Hankalinta ne ya tashi ta zauna dangalgal a kan farar kasar dake tsakar gidan muryarta na rawa ta ce" abana, ba abinda kake tunani kaina bane, aba ni kaina sun fi karfina ban san lokacin da aka mayar da ni wajen nan ba, hasalima ko asibitin gwanatin bani da damar ki dole na yi biyaya ni da bani da karfin komai, Ka yafe min wly ni bana wata soyaya da mutumin nan, dan wajen aikin mu hasalima wata magana bata taba hada ni da shi ba, Aba ka yafe min kar ka yi fushi da ni Ajiyar zuciyar da bai shirya ba ya sauke, sai kuma wani mugun tausayinta ya darsun masa a zuciyar sa, harma ya fara jin kunyar abinda yake son fada mata, ta inda zai bi ya fada mata Mariama ce ta fito ta nufo inda suke tana fadin" malan lafiya daga dawowar mu yarinya da danyen jiki ka saka ta kuka? Lallana lafiya? Dago da kansa ya yi yana kalon ta, murmushin takaici ya sakar mata ya sauke ajiyar zuciya ya kali Rauda ya ce" Raudana, a jiya na yi baban laifi, na yanke hukunci cikin fushi duda abin alkhairi ne na aikata aman ina cike da zulumin yanda zaki dauke shi Gabanta ne ta ji yana dukan tara tara, bata ce komai ba domin kafafuwanta har sun fara rawa dan kuwa a jiya tana tine a harzuke ransa a mugun bace ya fita a asibiti bayan ya yi furucin yau zai nuna ya isa da yayansa Idannuwansa ya rufe ya kuma budewa ba tare da ya kali Mariama ba ya ce" Rauda , *a jiya na daura maki aure* Ba rauda da Mariama ba , Aisha kanta sai da ta hantsula daga kan kujeea tayani tsegumi ta mike da mugun gudu ta karaso wajen iyayen nata da Rauda da ta sada kanta kasa ba wanda ya fahimci halin da take ciki Mariama cikin tashin hankali ta ce" aure! Aure fa kace malan? Kana cikin hayacinka kuwa? Ka ko san abinda ka fada? Wa ka aurawa ya ta? Walahi talahi baka isa ba malan! Walahi baka isa ba a me ka dauke ni? Na dauki cikin yar na raini abina na sha wahalar kayana ka tashi ka nuna min iyakata dan bakar zuciya irin taka? Dan aunty ta yi maganar nan ne zaka wani biye mata? A yanzu da muke murnar Allah ya bilo mana hanyar da zamu ci mai dadi ne ka yi min wannan danyen aikin? Dago da kansa ya yi ya ce" ki sasauta muryarki Mariama ki daina yi min ihu a kaina Aisha ta yi saurin zubewa a kasa ta ce" aba, aman ai banda ni ka daurawa airen ko aba? Da kallon tausayin halayenta ya bi ta, ya so ace a jiya ta samu wanda ya taya ta koda mai hucewa ne da ya daura mata shi , itama cikin kakausar murya ya ce da ita" *Baki samu mai so ba, aman da zarar na samu kema zan aura maki!* Malan walahi baka isa ba, haka kake so yayan nawa suma ka kaisu gidan da har sai fatar su ta dawo kalar tawa dan wahala? Mai na kashe maka da har ya jaza min wannan wulalancin malan? Me na yo maka a duniya da zafi haka? Wly sai ya saketa ko dan gidan uban wanene! Su duka basu ga lokacin da ya mike ba, har ya kawo wajen Mariama da take tijara tamkar zata daku da shi ya aikata mata abinda bai taba yi mata ba, abinda bata taba kawowa ranta ba zai iya aikata mata! Abinda ya girgiza yayan su su kansu sukai mutuwar tsaye domin Rauda kanta sai da ta mike tsaye jin saukar marin da Malan Ya shararawa Mariama Yatsarsa manuniya ya nuno mata , ya kada kai ya fice bayan ya dungurawa Rauda akwati a kusanta ya fice kwata kwata a gidan A hankali Mariama ta sulale hannunta dafe da kuncinta ta hade bayanta da garu wanda a daidai lokacin da gudu suka rukunkumeta kowace ta saki kuka, Aisha na borin fadin kar ta bari itama ya aura mata Wani bayan ga wanda take so kamar ta mutu Rauda kuwa kukan abinda ya salamo rayuwarta da irin yanda fitintinu ke bilowa tsakannin iyayenta da tausayin mamanta dan ta san auren su da abanta ba na duka bane auren soyaya ne aure ne na hakuri aman tunda yau har ya yi duka tabas ya daki gawa ne dan mai rai ya ji tsoro, tsoronsa da tsoron hukuncinsa suka cika mata zuciya da tambayar shin wanene mahaifinta ya aura mata? Mariama kuwa ta kasa lalashin yayanta, tashin hankalin da take ciki ya girmami tunaninta harma ta nemi hawayenta ta ji su a kafe, zuciyarta ce ke mugun buga mata tana yi mata sama da kasa lumfashinta yana fita da gagawa, muryarta na rawa ta ce" *innalilahi wa ina ilaihi raj.une! Na kai malan wajen da ya taba lafiyar jikina, saurin dago yayan nata ta yi daga jikinta murya a matukar raunane ta ce" AISHA RAUDA MALAN DUKANA NE YA YI?* .......................... *❣IDAN KA RAINA INDA KAKE❣* Na: *SAJIDA* *_LITATAFAN MARUBUCIYAR_* *_Duk Karyar kada_* *_Yar Mahaukaciya_* *_Neman na kaina_* *_Bani da zabi_* *_Daga tafiya daukar soja_* *_Idan ka raina inda make_* *🌈KAINUWA WRITERS✍🏼 ASSOCIATION*🤝🏻 ```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}``` https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation 2⃣4⃣ Aisha ce ta yi karfin halin cewa" mama, walahi Aba ya canza, abanmu mai hakuri yau harda duka? Mama ni dai kar ya yayi min aure da kowa kar nima wannan yar uwar taki ta jaya min mama ni *ELHAJ SUDAIS* nake so kuma da shi zan rayu Sai a wannan lokacin kuka ya zowa Mariama, ta dago hannunta na hagu wanda ta dafe kuncin nata da shi ta ce" a nan ya dake ni, a nan ya mare ni, bai taba yi min haka ba, ya kasance mai hakuri da dukan shirme na, ba zan iya tunkararsa da wannan magangannun ba, ni kaina a yanzu walahil azim tsoronsa nake Cike da mamaki suke binta da kallo, daman mamansu na tsoron abansu haka aman take shagalinta? Ko dai tana anfani da irin yanda baya iya yi mata komai ne take taka rawarta ba kida? Hannayen su ta gamo ta fi bada hankalinta ga Rauda ta ce" yau zan baku tarihin rayuwar mu, Da farko Ahmad baya so na ko kadan, ni ni na yi ta naci har ya saurare ni! Na taso a gidan mu mu biyu mata ni da aunty sai namiji guda musbahu . Mun kasance............................ta kwashe labarin rayuwar su da yanda ta fara son Malan Ahmad da irin wahalar da suka sha, da irin gatan da malan ya yi masu, bayan rasuwarsa irin neman da malan ya ringa yi dan kar na shiga wahala kar na sha wuya, a haka har na haife ku daga baya ya dawo faskare Malan bai taba ko da wasa shakunata da fuskar fada ba, ya kasance mai hakuri da ni! Raudat, na ji haushin hukumcin da malan ya dauka a kanki, aman a yanzu ni da kaina neman kaina nake! Ki yi hakuri idan ya sauko daga fushin nan da ya tafi sai mu tatauna na tabata zai warware maki auren nan Mama ni fa? Muryar Aisha ta katse mahaifiyarsu wace jikinta har ya dauki zafi, ta kasa yarda da hannun Malan ne ya kawo jikinta da niyar fada Ta ce" sai mu yi fatan Allah ya sanyaya masa zuciyarsa kar ya yi maki ke ma RAUDA kam a daskare take ta fada cikin tunani, labarin iyayenta ya birge ta sannan sun bata tausayi, daman iyayen mamanta da ran su? Sannan masu kudi ne sukai watsi da ita dan kawai ta auri talaka.? Oh duniya ina zaki damu, a yanzu kawai idan baka da shi ba lale ne a ganka da daraja ba Ta kali mahaifiyar su dake rarashin Aisha a kasan zuciyarta take aiyana to ko dan mama ta fito daga tsatson masu kudi ne ya sa ta daina gannin kokarin Aba a kan su? Ko shi ya sa ya kasance *TA RAINA INDA TAKE?* to aman ai *IDAN KA RAINA INDA KAKE INDA ZAKA YA RAINA KA* wannan gidan kadai rufin asiri ne domin mutane da yawa suna mararin gannin su a irin wannan gida, zaka ga mai arzikin yana bin gidajen haya Rauda kar ki saka abinnan a ranki kin ji? Kar ya dawo ya hadasa maki cuta daman ba gama warkewa kika yi ba, insha Allahu malan zai saurare ni..... (KO?) mai kake so duniya ta dauke ka? Ya kake so a dauki lamarin? Haba SUDAIS bayan ka san irin yanda sunnanka ya yi fice a nigeria ? A gidan nan waye bai tako ya zo dan yi maka ta.aziyar rashin matarka ba? Aman a ce ko adu.ar 40 ba.a yi ba ka shigo min da maganar ka yi aure? Mahaidiyar sudais ce ke fada tun karfinta bayan Humaira ta suma sun yayafa mata ruwa ta farfado tana rusa kuka, gefe guda kuwa Auta ce ta yi tsutsuru sai Hajiya kaka da Mahaifin Sudais Aman kai yaron nan mai ya kaika aikata irin haka a kasar mu ta hausa? Bayan ka san duniya da kin gaskiya baka gudun a yi maka wata fasarar daban? Hajia kaka ta furta haka tana talabo habarta Humaira ta ce" mai na yi maka Elhaj? Mai na tsare maka? Yanzu du kukan da ka sha da rashin baci da sauke gadon dakinka dan matarka ta rasu aman ka je ka kara aure da wurin nan haka? Ta juya wajen Momy ta ce" momy mutuwa zan yi nima, walahi momy ina jin zafi a zuciyata, mai na yi masa da zafi haka? Wa na kashe masa? Ni dai ba zan iya zama da shi ba ba zan iya zama da kishiya ba sai dai ya sake ni ! Momy ta kamo Humaira ta shiga rarashinta ta ce" kar ki furta haka, karki fadi haka Humaira, ba dai ke ba zai saka sai dai ya saki ita yarinyar da ya auran! Wannan wani irin tashin hankali ne kuma kai da kanka Dady ka yi ja gaban daurin auren? Ba zai yiwu ba ya jaza min zagi a cikin gari *TO KIN ZABI FUSHIN ALLAH KENNAN A KAN ZAGIN CIKIN GARI?* DADY ya furta da kakausar murya Ke yanzu daman fadan naki dan kar a zage ki a duniya? Du iliminki? Ku dai mata idan abu ya shafi kishiya ne ba zaku yi masa kyakyawan zato ba? Shi dai aure rai ne da shi kuma lokaci ne ! Hajiya ai kin ganni, shi yake daure masa yana rashin mutuncinsa, ki duba fa ki ganni Hajia "Momy ta karashe tana kara zabgawa Sudais harara Hajia ta tsuke dan bakinta ta rafka tagumi hannu bibiyu, ita kam bata san mai zata ce ba ko yanda zata kashe wutar nan ba, tabas ba wanda ya isa ya hana abinda Allah ya halasta, duniya kiwa ba.a iya iya mata du irin kokarinka na ka iya mata zaka gaza ne Auta ta dago kanta ta shagwabe fuska ta ce" momy please ki yi hakuri a bar maganar haka Momy ta hayayago mata ta ce" auta kaniyar ki! Na ce kaniyar ki , ke tashi ki ba mutane waje an ki a yi hakurin! Sudais dake zaune saman kafet, ya kurawa waje daya ido du wannan hayagagar da ake bai furta ufan ba ya yi gum tamkar ma ba dashi ake ba Ta kuma juyowa wajen sa ta ce" kai ba zakai min magana ba ka bar ni na yi ta yawan magana kennan? Sudais ya dago idannuwansa ya sauke kan mahaifiyarsa murya a cunkushe ya ce" ki yi hakuri momy, ki yi hakuri Daga shi bai kuma furta komai ba, ita kanta sai ta rage fadan aman Hulaira sai rusasa kuka take tamkar ranta zai fita tana rantse rantse Hajia kaka ce ta matso kusa da shi ta kamo hannun sa ta ce" tashi mu tafi, mu je ka konta ka huta Mikewa ya yi da hanzarinsa ya shige gaba daman abinda yake jira kennan wanda zai fitar da shi daga gaban mahaifiyarsa a wannan lokacin Suna fitowa ya daga kafa ya shiga sauri dan barin wajen Hajia kaka ta ce" kai ya haka? Ka tsayani mana, ka tsaya ka san fa tsoron hanyar nan nake ga nisan tsiya ga shiru tamkar kushewa, me ke damunka haka ne? Dan dakatawa ya yi ya juyo, wannan tsohuwar na son ta hadasa masa ciwon kai, a dan kufule ya ce" dababayi na yi maki ne? Ki daga kafarki ko na yi tafiyata abinda zai kama ki ya kama ki a hanyar Hajia kaka ta ja ta tsaya ta rike habarta ta ce" iye, ka ji dan nema, ai ni ba makauniya bace, Allah na tuba ni muna yan mata kawance fa na yi da Ina kika fito fada ina zaki fada mai kike fada, ni har ka gwada min karfi? Kai din karfin ne da kai dan kana ganninka jibgaga sai shegen tsayi da jiki a tunaninka zaka iya tsare min wani abin ne?? Solopiyo kawai Sudais ya girgiza kai ya yi kwafa ya yi gaba abinsa ya barta a nan, Shiru ta yi ta jima tana waige waige can ta juya tana tafe tana fada tamkar ta ari baki ta koma bangaren Su momy wanda tana shiga Humaira na fitowa ta yi tamkar ta bangajeta ta fice Yana zuwa rigarsa kawai ya iya cirewa ya konta rigingine ya zubawa siling ido Humaira ce ta shigo ba ko salama ta ja ta tsaya tana cika tana batsewa ta kasa ci gaba da zuba rashin mutuncinta kamar yanda ta fara a wajen su momy Baya ya juya mata ya ja bargo ya rufe jikinsa ya shiga tunanin abinda yake ciki, shi sai ma yake jin baya zumudin auren nan a yanzu ko dan ya ji halayan mahaifiyarta ne? Oh duniya yana mamakin irin yanda mutane son kudi ya rufe masu ido Asuba ta gari angon RAUDA🥰 yanda ta ga rana haka ta ga dare, Malan Ahmad bai kwana cikin gida ba, sam bai ko leko su ba har garin Allah ya waye Motsin yayanta suna shiga wanka ya saka ta mike dan dora masu zazafe Tana faman hasa wutar ya shigo da salama ciki ciki, Da sauri ta mike ta amsa ta shiga gaishe shi aman ya yi tamkar bai ganta ba ya ja ya tsaya kofar dakin su Rauda ya kirayi sunnanta Da sauri ta amsa ta zumbula hijabinta ta fito ta duka tana gaishe shi Yannayinta yake karantawa, kamin ya sauke ajiyar zuciya, a sake ya amsa mata tamkar ba abinda ya faru ya ce" akwati da na baki jiya su ne suturun da mijin ki ya umarta da ki dawo sakawa, sannan ya ce akoy takarda a ciki , sai maganar zuwa aiki ya ce akoy waya a cikin akwatin idan kin dauka zaki ga sunna daya a ciki sai ki kirayi number ya kaiki wajen aiki ya dawo da ke Kanta a kasa take dan dagawa mahaifinta har ya gama ya ce" Allah ya yi maki albarka , ya juya ya barta nan tsugune ya fice a gidan ya bar Mariama baki bude, ta shiga tambayar kanta " kai malan fushin nasa har ya kai haka? Raudat kuwa ta shiga wani hali, a kasan zuciyarta take tambayar kanta " wannan shi kuwa wanene? Yaya sunnan sa ? A ina yake? Anya kuwa zai yi adalci a rayuwa? Ya ba zai zo ya isar mata da sako ba sai dai ya aiko mata da mahaifinta? Komawa ta yi dakin ta zauna ta jawo akwatin ta bude Dadagawa ta shiga yi cike da al.ajabin wannan lamari, Dogayen hijabai ne da dogayen riguna bakake kirin ba komai a jikin su sga sheken kauri sai gam irin ta hannu da safa da kuma likaf! Cike da mamaki ta mayar da kayan gefe ta dauko wayar yar karamar nokia ce tsohuwa harda wani dan zare an daure ta, da mamaki ta juya ta dadaga kayan, sababi ne, sannan da gannin yadidikan zasu yi tsada, kuma basa warin gonjo, aman wayar ko a dari biyar da wuya a saye ta, mamaki ne ya kashe ta ta mika hannunta ta dauko takarda fara kar da ita an yi rubutu kamar haka.............. ......... *❣IDAN KA RAINA INDA KAKE❣* Na: *SAJIDA* *_LITATAFAN MARUBUCIYAR_* *_Duk Karyar kada_* *_Yar Mahaukaciya_* *_Neman na kaina_* *_Bani da zabi_* *_Daga tafiya daukar soja_* *_Idan ka raina inda make_* *🌈KAINUWA WRITERS✍🏼 ASSOCIATION*🤝🏻 ```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}``` https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation 2⃣5⃣ Lettern ya kunshi magangannu kamar haka: A yau na zo masalaci dan gabatar da sallar da ta kama ni a hanya na tarar da datijo ya zo da maganar zai aurar da yayansa *sadaka*, ina zaune ina kallo har kowa ya watse ba wanda ya taya, na jinjina abinnan harma na yiwa kaina tambayar *WHO ARE YOU* haka da har *bakin jini* ya yi maku mugun shiga? Ko kuwa *Munin ku ne ya yi yawa?* ko kuwa kun *tsofe* masa ne a gida ba mashinshini? ko dai *HALAYAN* ne sai a hankali? *I don.t know🤷‍♂* gannin du an watse an bar shi *Tausayin* datijon nan ya saka na kasa tashi sai da na karbi *tayin sa* aka daura min aure da karamar mai sunna *RAUDA* *ASALAMOU ALAIKI RAUDA* ni musulmi ne, wanda ya san darajar aure, koda kuwa ban sanki ba dole ne na fada maki cewa ina kishin du abinda yake nawa! *RAUDA YOU ARE MINE!* an aura min ke ina so ki kare min mutuncina kafin na bada lokacin da zaki zo gidana da matana domin ba ke daya bace, Mahaifinki ya shaidan kina aiki dan samun kudin makaranta, bani da damuwa da *NEMAN NA KANKI* da kike a yanzu aman ban yi maki alkawarin zai dore ba, ga tufafi ki yi anfani da su,su ne zabina indai zaki tsalake soron gidan ku, idan da magana sai ki rubuta ki baiwa Malan zai bani! Kar ki manta *AUREN HADI* aka yi, *BIYAYA* wa umarnina ya zama dole. Ta maimaita karatun wasikar nan ya fi a kirga har Aisha ta yi tafiyarta tana mitar bata gama ba Firgigit ta yi kamar wace aka zubawa ruwa a jikinta ta jujuya takardar tana tunani, ita fa daga jiya zuwa yau ta kasa gane a raye take ko a mace? Takardar ta kuma budawa dan sake karantawa sai ji ta yi wasu zazafan hawaye sun wanke mata fuska, Kanta ta kifar a jikin bed dinta ta saki wani dan marayan kuka wanda yake fitowa da kyar domin muryar ta a shake take sosai A fili ta furta" *WHO ARE YOU 2?* ya aka yi ka iya zarowa mutun dan adam zafafan kalamai haka dan Allah ya hada ka da shi? Ka yi hakuri, kar ka koya min baudadan halaya domin nakan koyi yanda mutun ke son zama da ni ne, ka yafe min *ka sake ni* domin ni ma bani da sanayar za.a hada ni aure da kai da na kiyewa wannan kudiri! Ta dan jima kamin ta mike ta goge idannuwanta ta saka doguwar rigar ta zumbula hijabin sannan ta saka safar hannun da na kafar gaba daya bakake ta dauko nikaf din ta dauki yar wayar ta latsa kira aman har ta mutu ba.a daga ba Gannin ta kusa minti ashirin tana jira kawai ta dauko pos dinta ta fito ta yiwa mahaifiyarta salama jiki a sanyaye ta fita inda mariama ta bita da kallo Tana fitowa abin mamaki ta ga wata mota kofar gidan baka da bakaken madubai sannan kamar ta mugun jin jiki kamar an yi accident da ita dai, Hon aka yi mata sannan flashing ya shigo wayar dan haka ta nufi motar gannin an bude kofar bayan dukan alamu suka nuna ita ake yiwa magana Asalamu alaika malan ko kai ne aka turo ka kai ni wajen aiki? Rauda ta fada tana kallon direban da fuskar sa ke kallon wajenta aman idannuwansa a sade Kansa kawai ya iya daga mata alamar eh sannan ya yi mata nuni da hannun sa Da mamaki take kallon sa, a ranta ta ayanna" wayo bawan Allah ashe kurma ne, aman yana ji, to aman ya aka yi ya hada ni da direba kurma? Wani irin tuki zai yi? Kafadunta ta daga ta dan yi murmushi ta ce" aa ke kuwa Rauda ai yana ji yana kuma gani maidawa ne baya yi dan haka zai ji hon din wani sannan zai gani, komai dai sai Allah ya yarda dan haka Allah kare mu Shiga motar ta yi ya ja bakinsa gum bai furta ko a ba Suna zuwa ga mamakinta zarcewa ya yi, masu tsaro basu wani tare shi ba, aka wangame masu get motar ta shiga da su, sai da ya kaita har bangaren da zata hau ta nufi office din su ya sauke ta, Ta sauka tana al.ajabin wannan mutumin da aka aura mata ko waye ya yi mata farin sani, dan ba zai ce mahaifinta ne ya fada masa wajen aikinta harma da kofar kofar aikin nata domin shi kansa bai sani ba Shi kuwa direban yana ajiye ta ya juya wajen samir dake tsaye kusa da motarsa yana kara jadadawa cewa idan ta zo kar wanda ya hana ta shiga da irin shigar nan tata umarnin oga! Domin a ma.aikatar ba.a shiga da irin wannan kukuf din ko da nikaf dan gudun mugaye Yawa Adahir fatan ka kula da dokokin oga Wanda aka kira da adahir, wato direban Rauda ya yi murmushi da mamakina ya ce" haba Elhaj, ai koda cewa aka yi na yi tuki a konce zan yi balatana wannan ai a kurma ma ta dauke ni kuma insha Allah ba zan taba yi mata magana ba kamar yanda oga ya hana ( to ka ji) Malan Ahmad ne zaune kasan shukar maina , faskarensa gefe ajiye, sai bakar ledar da ya anso shinkafa da wake lwajen laure mai tuwo ya tisa ledar ya kasa ci" a fili ya furta ko mai zasu ci yau? Ajiyar zuciya ya sauke ya dago hannun nasa na dama dan cin abincin sai dai ya tsaya tamkar an tsayar da shi ya tsurawa hannun nasa ido, a fili ya furta" da wannan hannun ne na mare ta! Da wannan hannun na mare ki Mariamna, kin ga kin ja na kaucewa wa.azi cewa idan matarka ta bata maka rai har ka yi niyar dukanta ka dake ta a bayanta (duwawunta) dA karan tsintsiya aman ke kin saka na gabza maki hannun gardi ko? Na biyu kin ja na taba lafiyar jikin ki wanda har wajen adu.ata nake rokon Allah ya bani ikon gama rayuwana ba tare da na taba lafiyarki ba ko? Mariamna kin ja na hukunta baiwar Allah, har na shiga zulunmin wani hali zata shiga? Shin mutumin nan mai kudi ba zai wulakanta min Raudana ba? Mariamna ya fuskar ki? Fatan bata haye ba? Kin ga kin saka na zama abinda ba haka nake ba, aman dole na hukunta ku, dole na nuna maku ni na san darajar kaina! Can kuma ya js numfashi ya ce" Raudana, Allah ya baki farin ciki mai dorewa, ya sa halayen ki na kwarai su zamto silar shigar ki farin ciki, ya sa kar ki canza hali har zuwa kushewar ki.......... Tana shigowa mai goge goge wato Rabilu ya gaishe ta aman kansa a kasa Da fararan idannuwanta take kalon sa ta amsa shi muryarta a shake , ta juya da niyar hawa matatakalar da zai sada ta da office dinta sai dai da mamakinta sai ya nuna mata accensaire🤨 din Elhaj Sudais ya ce" *HAJIA* an bar salahun idan kin zo ki daina bi ta nan ki bi ta cikin nan ya hauda ke, sabon tsarin da aka fido ne Mamakinta ne ya ragu, duda ta san ba mai shiga sai shi kadai, shi dinma idan baya zagaye, aman jin sabon tsarin gidan ne sai ta juya ta dana ya bude ta shiga bayan ya shaida mata numbe 9 ne daidai office din su a ranta take ayanna " *oh na aunty AISHA sarkin iya yi, ya dai saka muma har mun ji dadi mu tsufa da kafafuwa Kokowa yake da zuciyarsa tunda ya ga fitowarta ta nufo office dinta, tsale zuciyar sa ke yi tana murnar ta ga abincinta , ingiza shi take da ya fito da gudu ya yi mata oyoyo ya tarbe ta ya rungume ta a kirjinsa ya fada mata *how yake son ta* Mikewa ya yi da saurinsa da karfinsa ya tunkari kofar office din sa ya kama kamar zai bude , ya koma.... Ya kuma tasowa ya koma ya zauna ya hade bayansa da jikin kujerar ya dafe daidai zuciyarsa dake yi masa kida tammar zata bala kirjinsa ta fito Tamkar zarare a fili ya ce" haba SUDAIS, kar ka manta da irin yanda ka yi niyar zuwar mata, kar ka manta sai ka san wacece ita kafin ka yi mata tayin so, dan haka ka daina irin wannan bayar da kan naka har ta fahimci abinda kake ciki Lumshe idannuwansa ya yi, ya yatsina fuska tamkar wani ne ya yi masa maganar sai ya baiwa kansa amsa ya ce" ka gane abin ne zai yi matukar wahala gani ga *MATA* a matsayin matata aman bani da damar nuna mata ? Akoy damuwa domin ina sonta da yawa.... Ya shagwabe bakinsa ya kontar da kansa domin wata muguwar kasala ce ta shiga jikinsa lokaci guda, Wayarsa ce ta dauki kara dan haka ya bude idannuwansa dake lumshe ya mika hannunsa ya janyo wayar ya daga ya kara a kunnen sa bai yi magana ba Samir da ya tabata yana jin sa ya ce" oga, Direban ya bi dukan dokokin da ka dora Alhamdulilah ya kawo ta lafiya Samir ya yi shiru ko zai bashi amsa aman shiru har kusan minti biyu kuma ba.a kashe wayar ba, Dan haka ya ce" oga ko baci kake? Sudais murya a can ciki ya ce" samir, ba zan iya wannan tsarin ba, *INA SON ABINA* kuma zan tafi na fada mata yanzu ... Wata irin zabura samir ya yi cikin gagawar murya ya ce" aa, aa, aa Ka saurare ni kar ka aikata haka , ka tuna dalilin da ya sa ka ce zaka yi mata haka, kar ka manta kana son sai ka ware zare da abawa..... Samir na cikin magana karaurawar office dinsa ta dan yi kara irin na neman izinin shigowa Firgigit ya kali saman computersa dan gannin ko waye domin ya shagala bai ga zuwan kowa ba Mikewa ya yi tsaye hannayen sa suka kwashi bari, muryarsa kanta rawarawa take ya ce" Samir...... ita ce.... Bai tsaya ya ji amsar samir din ba ya..... *❣IDAN KA RAINA INDA KAKE❣* Na: *SAJIDA* *_LITATAFAN MARUBUCIYAR_* *_Duk Karyar kada_* *_Yar Mahaukaciya_* *_Neman na kaina_* *_Bani da zabi_* *_Daga tafiya daukar soja_* *_Idan ka raina inda make_* *🌈KAINUWA WRITERS✍🏼 ASSOCIATION*🤝🏻 ```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}``` https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation 2⃣6⃣ *MOM KHALEED GODIYA MAI TARIN YAWA ZUWA GARE KI, NA BAKI PAGE DIN NAN KYAUTA KI YI YANDA KIKE SO DA ITA, COMMENT DIN KI NA SAKA NI NISHADI* Bai tsaya ya ji amsar Samir din ba ya datse kiran, ya zabura ya shiga gyara doguwar jalabiyar dake jikinsa mai ruwan ash kala, ya gyara hiraminsa ya dauki papier ya goge agogon hannunsa mai ruwan ash color mai haske, ya dauki turaran sa dake ajiye saman table dinsa ya kara yiwa jikinsa wanka da shi ya koma kan kujerar ya hakimce ya hade fuska ya dana bouton din dake bude kofar Sanyayan kamshi hade da mugun sanyin ac ya watso mata wanda duda uwar shigar nan ta jikinta sai da ta ji sanyin nan, ita kam tana mamakin wannan mutumin ko dan yana zaman saudiya ne? Sanyi baya ce masa komai Muryarta a shake ta ce" morning sire Bai iya dagowa ya kale ta ba ya daga mata hannu cike da basarwa , aman kasan zuciyarsa yana tambayar sa mura take? Mai ke damunta? Mura? Muryarta a shake ko dai kuka ta yi? Gabansa ya bada ris, kuka? Kukan me ta yi? Na bata son aurensa ko me? Takardun hannunta ta ajiye saman table, ta dan gyara muryarta ta ce" sire ga takardun nan Dago da fuskarsa ya yi cikin wani irin yannayi da rashin nutsuwar jin kalar muryarta ya zuba mata idannuwansa su ba jajaye ba su ba farare ba an yi daidai itama ta kalo wajen sa, wani irin abu take ganni a idannuwansa tamkar mai galla mata harare hakan ya sa ta yi gagawar sada kanta jikinta na kyarma ta fara kokarin kunce nikaf dinta domin ita a tunaninta ko dan nikaf din ne yake harararta Kasa kifta idannuwansa ya yi daga kanta, har ta cire nikaf sin ta cukuikuye shi a hannunta sannan ta shiga cire safar wanda hakan ya baiwa fararan hannayenta damar bayana Kanta kasa murya na rawa rawa ta ce" ka yi hakuri, nnnnna , an hana ni yawo ba su ne ka yi hakuri Sire ....tana maganar ne tana cike da tsoron sa, tsoron kar a je ya dauki mataki a kanta sanadiyar saka nikaf a ma.aikatarsa harda safa, hijabin kansa yayi girma da yawa kan ka.idar kampanin Ajiyar zuciya ya shiga saki, muryarsa ciki ciki ya ce" ki mayar da abinki Da sauri ta dago ta dan kale shi, ta kawar da idannuwanta tana mai godiya da Allah da ya fahimci manufarta ya taya ta yiwa mijin da bata sani ba biyaya Takardun ya shiga dubawa yana saka hannu, kasa kasa kuma yana satar kalonta , ta hadu da jikin garun office din kanta a kasa sai murza hannayenta biyu take A kasan zuciyarsa ya ambata " bata cikin farin ciki Aman menene dalilin shigarta damuwa? Karar kofar ya dawo da shi ya kali wajen ya ga Samir ne, Kallonta ya yi da kyau ya ga ta mayar da komai dan haka ya danna samir ya shigo ya gaishe shi ya ja ya tsaya masa Kansa ya girgiza dan ya san manufar samir, ya bata izinin tafiya Da dan sauri ta fice ta shige office dinta, tana shiga ta zauna tana sauke ajiyar zuciya, a fili ta furta" ashe yana da dan fahimta ? Allah na gode maka da hakan bai jaza min damuwa ba dan idan ya nace sai dai na bar aikin bana son abinda zai batawa mahaifina rai Tana fita ya maido kalon sa wajen Samir, da girarsa ya yi masa tambayar lafiya? Samir ya sauke ajiyar zuciya ya ce" oga ka ce idan na ga zaka fada mata sirrin dake ranka na yi gagawar tunasar da kai dalilin da ya sa zaka fito mata a ba kai ba dan kar a je ka fada kuma bata zama yanda kake so ba Sudais ya yi murmushi ya ce" ta saka kayan Samir, ta yi yanda na fada mata Samir ma ya yi murmushi ya ce" Allah ya sa ta mutunci ce mau halub mutunci Bayan salar isha.i Fitowa ya yi ya zauna saman table dinsa, yana amsa waya da chairman suna maganar sabin kayan da zasu shigo a satin nan, Kwaliya ta sha , iya kwaliya ta fito tana yauki ta nufo inda yake zaune ta zauna ta bubude abinci ta dibar masa nasa ta zuba masa miya , ta suba masa salak gefe ta gyara masa komai abinda bata taba yi masa ba Wayarsa ya gama ya mika hannunsa ya dauko salak din ya gyara shi ya yi bisimillah ya dan fara ci Yana gamawa ya sha jus din na kwali wanda shan sa ya zame masa dole Bai tashi ba kuma bai yi magana ba har ya ga ta gama cin abincinta ta sha ruwa ta yi gyatsa Murya a kausashe ya ce" jiya kika ce na sake ki? Da sauri ta dago da kanta gabanta ya mugun fadi, ita ta san daman ba mantawa yayi ba, kamar yanda ya saba ne idan sun bata masa rai baya magana a lokacin sai ya kwana , wani lokacin har sai ya yi tamkar ya manta sannan yake taso maganar dan kuwa gaskiya ya fiya bin dindigin abu , ta tuno yanda suka yi da mamanta a jiya inda take yi mata fada ta ce ai sai ki balo auren ki dawo mu jera, kina gani tunda kika yi aurennan ba ni ba mahaifinki kansa ya daina bautawa gwamnati muna morewar mu mu wanke goma mu tsoma biyar, ai sai na fadawa Elhaj zaki balo auren dan haka maza ya fara neman aiki dan kin san sai an ci abinci za.a rayu banza marar tunani, ke bai sake ki har ke zaki nemi saki? Kar ki manta daga gidan kara muka koma na bulo, wuta ruwa yan aiki salary na du karahen wata sai managensa ya kawo mana , ki ce na fasa kuna ac dan na kusa daina sha na dawo zaman rana banza , Firgigit ta yi ta kalo shi, ita kanta a yanzu ba zata iya zama wajen da ba ac ba dan ya saba mata rayuwar luxe Murya na rawa ta ce" ka ka yi hakuri dan Allah Tsareta ya yi da ido, can ya yi kwafa ya mike, Har ya fara tafiya ya dawo ya ce" momy da dady ne kadai suke da wannan pride din ba ke ba, u'r my wife ba mom dina ba so be careful! Yana gama fada ya juya abinsa ya tafi ya barta da ciza yatsa Malan na bata ambelope fara da sako wanda ya shaida mata inji mijinta, ya juya da niyar barin gidan Da mugun sauri ta biyo bayansa har tana tuntube ta ce" malan, malan , malan.... dan girman Allah ka saurareni Cak ya tsaya ya juyo yana kallonta, Ji yake tamkar ya shekara bai ji muryarta ba, Allah yana gani tun baya sonta har ya dawo ya fita sonta aman halayenta suna neman mayar da shi wani kala Malan ya haka? Jiya baka kwana gidannan ba, yauma kana faman ficewa, da alama fushin nan naka na neman sakaka ka sabawa Allah , kar ka manta hakokinmu dake kanka Murmushin takaici ya sakar mata, wai shi zata fadawa haka, shi da ya san wannan shirmen zata fada masa ai da bai tsaya ba, hannayensa ya watsa ya ce" kinga kuwa bai shafe ni ba, hakinki bani da shi, kin ga ni talaka ne bani da abin baki, dan haka ki je wajen yar uwarki ta ciyar da ke Yana gama fada ya fice yana nema mata shiriya a cikin ransa (mata , wani lokacin mu ne masu jazawa kanmu damuwa, mu ke koyawa mazajen mu muguyen halaya, idan sunai mana kokari bama gani har su dawo su daina! Uhum Allah ka sa mu dace) Wajen Raudat ta koma, wace ta yi wanka aman jikinta har yanzu dumin suturar da ta wuni da ita bai bar jikinta ba, ita har ji take gumin na fita da wani laushin fatarta ( sirrin lulube jiki, bayan bin umarnin Allah da mazon sa, kare mutunci a cikin al.uma, samun daraja, harda gyaran jiki domin fatar ki ba zata bushe maki ba!) Mama ce ta shigo ta ce" wai ni Rauda menene Malan ke shigo maki da shi? Ta dan kawar da fuskarta ta ce" sako ne wai daga wajen mutumin da ya aura min Aisha ta ce" hum mama wai kin ga magangannu na rashin mutunci? Ko waye wannan mutumin bashi damutunci magangannu haka gatsaigatsai Rauda ta kallota da mamaki, ta ce" Aunty, ke kuwa a ina kika ga haka? Aisha ta ja tsaki ta ce" daukowa na yi a cikin kano ta yi zahin ki, na karanta dan na ga harda su letter may be wani baban ne sai dai na ga lettern da hausa na ga javaliyan magangannunsa na yaga ta Rauda ta girgiza kanta ta mike da ambulope din ta daina budewa danma kar ta kuma saka mata ido, ta lura sai fa ta jajirce zata samu damar yiwa mahaifinta biyaya dan kuwa idan dai zata ci gaba da sauraron su Aisha ne ba zata ga da kyau ba Da asuba ta buda ambelope din ta duba, sai da gabanta ya fadi domin sababin yan dubudubu ne har ashirin, Da sauri ta mayar ta rufe jikinta na kyarma ta dauko takarda da alkalami ta zauna ta yi rubutu kamar haka " *YAR SADAKA CE* Sannan ta saka a leda ta zauna har gari ya waye ta baiwa abanta ya ba mutumin nan, tap ita ina zata shiga da kudi har haka? Ya Allah ka sa ba wani mugu bane wannan bawan Allahn Yauma kamar jiya shigowa ya yi ya leka su, da Sauri Rauda ta duka ta baiwa mahaifinta ledar kanta a kasa bata iya cewa komai ba dan nauyin ta cewa babanta ya kaiwa mutumin nan sako take ji Murmushi ya yi ya juya da ledar ya fita, Samir dake zaune yana jiran fitowarsa ko da sako ne ya karbi ledar yana godiya ya juya A layi suke suna shiga office din da ake biya masu dauka a nan , wasu kuwa an zuba masu a account din su har sun sami alert, Tana faman ta yi ta gama ta fito Basma ta shigo tana ta murmushi ta zauna tana ambata Wash na gaji da yawa Rauda ta kaleta da murmushi a fuskarta ta ce" ai shi yasa nake so idan an dan rarage sai na je na karbo nawa, Basma ta yi murmushi ta ce" ai ga naki, an karbo maki Rauda ta kaleta , tana shirin tambayarta wa ya karbo mata sai ga Aisha ta shigo da murnarta Zama ta yi gaban Rauda ta nade kafafuwanta ta zazago kudin daga jakarta fara Ido Rauda ta zaro bakinta har bari yake ta ce" sisister wannan uban kudin fa? Aisha ta mike ta shiga kwaso shoki tana juyawa ta ce" dubu na gugar dubu sai da aka bani dubu dari da hamsin, tawa , ta kaina🤣, ni kam na daina.karatun wannan salaryn ya ishe ni kafin na malaki wurin... Rauda ta yi gagawar bada zancen ta ce" Allah mai kyauta da kari, yau yau akoy murna shikennan na makaranta ya samu Aisha ta yatsina fuska tana tatAra kudaden ta ce", makaranta? Ke da akai maki aure ki tanaji kayan daki da kicin mana daidai karfin ki.....ni kin ga tafiyata Ta juya ta fice ta bar Basma da sakin baki Juyowa ta yi ta ce" wai da gaske take an yi maki aure? Jikinta ne ya yi sanyi gannin yanda hawaye ya zirarowa Rauda, da sauri ta share ta kakaro murmushi Basma ta sako wani zancen dan gudun shiga iri yanmayi Ya shiga rudannin kalmomin Rauda, ba wata doguwar magana kawai ta rubuta masa *YAR SADAKA CE* me take nufi? Ya Allah ka bani ikon dawo da jarumtata a kan yarinyar nan Mikewa ya yi ya fito sai cin karo suka yi da Aisha, Cike da murmushi ta tunkare shi wanda hakan ya saka shi faduwar gaba ya ja ya tsaya shi ba ya juya ba shi ba ya tafi ba Ina kwana yaya! Aisha ta fada tana kara kunace masa waje Hade fuskarsa ya yi tamkar bakin hadari, daidai nan su Rauda suka fito ita da Basma Gannin Aisha na kokarin taka dokar da aka yi mata kyakaywan kashedi da kuma kuma horon canza mata wurin aiki aman har ta manta ta rike dubu dari da hamsin dinta a jaka tamkar ta kwaso kudaden banki gaba daya Da sauri ta matso ta kama hannun Aisha ta ce" i bg u mu tafi Aunty Aisha ta janye hannunta da karfi ta ce" a yau sai dai idan korar tawa zai yi ya yi, Tana gama fada ta juyo wajen Sudais da ya juya da sauri dan komawa office dinsa yana adu.ar neman tsari wa fitinar nan sai dai me hannunsa Aisha ta damko da karfinta ta yi gagawar matsawa sosai kusa da shi A mugun harzuke ya juyo ya sauke mata idannuwansa da sukai jajajir lokaci daya Aisha ta fashe da kuka ta ce" har yaushe zaka daina yin tamkar bana raye? Har yaushe zaka mayar da ni mutun irin na kowa? Har yaushe zaka lura da ni ka gane halin da nake ciki? Saurin rintse idannuwansa ya yi, murya a kausashe ya ce" ki fita a wajen nan Mahaukaciya tun kafin na koya maki hankali na baki tarbiyar da kika rasa! Da sauri Rauda ta rintse idannuwanta jin tun ba.a je ko.ina ba Aisha ta jaya iyayen su zagi, domin dai tarbiya ai iyaye ke bayarwa ko? Idan ya ce haka kennan iyayenta basu bata tarbiya ba? Ranta ne ta ji yana tafarfasa Aisha ta share hawayenta ta ce" koma mai zaka ce ni ina Son k......mmm Kafin ta karasa fitar da garafin karshe wato Ka..... ta ji gaba daya jinta da ganninta sun dauke na wucin gadi Luuu ta yi zata kai kasa aman kafin ta fadin ta ji karan saukar wani lafiyayan marin da ya saka ta sakin dan fitsarin da take rikewa, Mari ne, mari ne, wa yayi marin? Rauda ce ta sakar masa mari a gefen dama, rauda ce ta takarkare ta sakar masa marin da ya saka Basma , Aisha, Da Samir daura hannayen su bibiyu a saman kansu, tsoro, firgici , da mamakin abinda ta aikata ya saka Samir furta tun karfinsa" *NA MUTU* Idannuwanta cike da kwala ta watsa albashin da aka bata na tsawon aikin wata guda da ta yi , daidai hawayenta sun sami damar fitowa a kwarmin idannuwanta ta nuno wajen da yake da dan yatsarta ta ce" Wayo 😳😳😳 , Mari, wai wama ta mara tukunnan? Ya kuke gannin za.a karke? Cmment😟😟😟 Readers, me nufin Rauda ne da kalmar " *YAR SADAKA CE?* shin ta raina kokarin mijinta ne ko ta riki maganar a ranta? Ya kuke daukar novel din nan? A fa yi hakuri da mu yan koyo ne🥰🥰🥰 *❣IDAN KA RAINA INDA KAKE❣* Na: *SAJIDA* *_LITATAFAN MARUBUCIYAR_* *_Duk Karyar kada_* *_Yar Mahaukaciya_* *_Neman na kaina_* *_Bani da zabi_* *_Daga tafiya daukar soja_* *_Idan ka raina inda make_* *🌈KAINUWA WRITERS✍🏼 ASSOCIATION*🤝🏻 ```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}``` https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation 2⃣7⃣ Ta ce" dan yaya sun aikata laifi sai a zagi iyayen su? Kai ka san su waye iyayen namu ko ka taba haduwa da su da har tunaninka ya baka darajar su ko girman su daidai yake da naka kana iya takawa? Jajayan idannuwansa ya dago ya sauke a kan fuskarta, mari? Marinsa ta yi? Mari? Mace ce ta mare shi, abinda ba.a taba yi masa ba tun daga farin wayon sa har zuwa yau, ko kwalar rigarsa ba.a taba shaka ba, aman a yau mace, karamar yarinya , wace take matarsa ce ta daga hannu ta mare shi! Kansa ya ji ya wani irin sara masa, nan da nan jijiyoyin kansa wuyansa da hannayensa suka firfito sukai rado rado ana kalon su a fili, Wayar dake hannunsa ce ya rike irin rikon da koda kashin mutun ne zai karye ne, wannan babar wayar iphone din sai ji kake bak bak tana fashewa sannan maduban na shiga lalausan tafin hannunsa sai jinni ya fara dan tsagowa yana daso a wajen Samir da jikinsa ke kyarma ya kwaso da gudu ya bude office din Sudais ya shiga kokarin tura shi aman ko gezau baya yi Da mugun sauri Basma ta janyo hannayen Rauda, wace ta yi mutuwar tsaye kuma wani mugun tsoro ya darsun mata, Janta take tamkar ana jan rago da igiya, suna fitowa Rauda ta kali gabas da yama , kudu da arewa, hanayenta ta dora saman kanta ta fasa kuka, a fili take fadin" na shiga ukuna ni Rauda zuciya ta debe ni na janyowa kaf zuri.ata barin nigeriar kanta bama garinnan ba, wayo Allahna wayo ni raina mai ya kaini aikata hakan? Basma ki taimaki rayuwana ki mayar da ni ya kashe ni idan dai zai bar hukuncin iya ni, wayo ni kaina da aurena na taba fuskar wani katon dan fushin zuciya, ashe bani da nutsuwa har haka? Ya zamu kare da auntyna a yau ni Rauda? Kasakai Basma ta yi tana kallon ta, da harshen turanci ta ce" Rauda, dama cikin hankalin ki kika kai hannayenki kan fuskar Elhaj SUDAIS mai daraja? Ke kuwa kin san ko shi waye a fadin duniya ? Najimi ko yaro ne zaka ji tsoron aikata irin haka a gare shi Rauda Rauda ta kara tsorata da abinda Basma ta fada, da saurinta ta juya ta fito bata ma san abinda take yi ba ta tsayar da mai mashin ta hau cewa kawai take mu tafi, mu je Da kyar Samir ya samu ya tura Sudais aman bakinsa kan kofar ya ja ya tsaya Samir ya rasa ya zai yi, mai zai ce? Tsayawa ya yi jikinsa na dan bari muryarsa na rawa rawa ya ce" ooooga ka ka zauna dan Allah Idannuwansa ya dago ya sauke kan fuskar Samir, ya yi masa kallon da ya kai na minti biyar domin Samir har ya fara fida rai da zai amsa masa , can cikin murya mai amon zaki ya ce" ka bita, ka tabatar ta an kaita gida Samir kwalalo ido ya yi, na bita? Yake tambayar kansa, ikon Allah na bita fa ya ce? Yanzu du irin marin da ta daga hannunta ta sharara masa shine zai budi baki ya ce na bita? Ko a tarihin yarintarsa ana danganta shi ne da dutse wato dunkum da shi sai ta baci zai kai naushi, ikon Allah mace ce, ta mare shi kuma yake ambaton a tabatar masa da ta tafi gida Samir ba fita Sudais ya karasa jikin madubin office dinsa ya tsurawa wajen ido, a hankali ya sa hannunsa na dama ya shafa gefen fuskarsa, ya kuma shafawa, ya bi jijiyoyin jikinsa da kallo, ya dago dara daran idannuwansa ya sauke a kan fuskarsa kadai, A fili ya furta" *Marina* Juyawa ya yi ya dauki ky din mota da yar karamar waya still hannunsa da abin jini jini ya fice a office din Direct wajen zaman mahaifinsa ya nufa, yana zuwa ya ja gaba da su kadan ya tsaya Da kallo suka bi motar suna jira ya fito, domin ya saba idan ya zo gaishe da mahaifinsa yakan fitowa ne ya haisar da kowa cikin raha su dan zazanta harkokin yau da kulun kafin ya koma aman yau yana neman kwasan dogon kiwo Malan Shehu mahaifin marigayiya ne ya ce" aa, kamar Elhaj? Kuma bai fito ba ko dai lafiya? Ko waya yake? Dady da ya tsurawa motar ido, gaba daya jikinsa ya bashi ba lafiya dan haka ya mike bai ce komai ba ya karasa ya bude gaban motar ya shiga yana kallon wajen sa Gabansa ne ya fadi gannin yanda kwatakwata ba alamar nutsuwa a tatare da SUDAIS, sai kuma abin jini jinin da ya ji ciwo da yar sauran kwalbar da ta shishige masa hannu..... Da sauri ya kima kallon fuskarsa ya ce" hadari ka yi? Sudais na kallon sa bai iya cewa komai ba, Dady ya ce" ba zaka amsani ba? Mai ke damun ka haka? Sudais ya kifta idannuwansa, yama rasa mai zai cewa mahaifinsa, ahi dai abu biyu ya sani idan ya zo wajen mahaifin sa ba zai bar shi aikata mugun abu ba, sannan ya tabata da zai sama masa nutsuwa Ajiyar zuciya Dady ya sauke, shi kam Allah ya bashi bahagumen yaro ace abun damuwa na damunsa aman ba zai budi bakinsa ya fadi damuwarsa ba sai dai ya tsare mutun da ido koda kuwa wuni zaku yi da shi a haka? Shi kam yana gannin ikon Allah sai adu.a Hannunda ya mika wajen kuna wakokin motar sai dai sabuwa ce baya gane systeme dinta Fita ya yi ya dauko wayarsa ya dawo ya shiga motar ya zauna ya kunna karatu Shima jingina yayi da kujerar motar kamar yanda Sudais ya yi .. A kadan sun kwashi minti arba.in a haka kafin ya dago ya kalo Wajen Sudais sai ya ganni yayi baci yana sauke ajiyar zuciya Da dabara ya samu ya matsar da shi kujerar kusa da mai tuki ya gyara masa konciyarsa bayan ya kontar da kujerar Wajen direba ya shiga ya zauna yana adu.ar Allah ya sa motar auto ce, aman da kamar wuya wannan galeliyar motar ace auto ce Ai kuwa yana gyara zamansa ya kunna ya ga Auto ce, dan murmushi ya yi ya tayar da motar ya nufi gidan Sudais Wanda yake cikin gra gidan da bai jima da gama gina shi ba Wohoho zo ku ga gini har gini, gida har gida, ginnin gidan nan baki ba zai fadi tsaruwarsa ba, ya tsaru , ya ginu, an kashe kudi tamkar ba zai zama kasa ba, tamkar ba za.a mutu ba domin irin ginnin nan mai karamin imani baya zama cikinsa🤦‍♀ Hanyar kasa ce da ta sama , pave ne shinfide a ko.ina, Bayan shigarsa sai da yayi tafiya mai nisa kafin ya samu ya tsayar da motar daidai kofar da zata haudasu bangaren Uban Masu gida Da kyar ya samu ya dan farka daga bacin da ya tafi, ya talabo shi suka fito suka nufi accensaire din Dady ya mugun gaji kafin yake samu ya shigar da shi ya shinfide shi saman lalausan kafet din wajen A hankali ya zauna kusa da shi ya riko hannunsa na dama yana tofa masa adu.a har shima ya fara gyadigyadi san haka shima ya konta sai baci Dan motsin kamar cokali ya farkar da shi a bacin da ya afka Yana farkawa ya ga Sudais ne zaune yana motsa kofi a cikin cop Hamdallah ya yi a cikin ransa, ya mike ya tafi cikin daki guda dan shiga bayi Ya jima kafin yake fitowa ya tada sallah dan kuwa har karfe hudu ya yi, Yana gamawa Sudais ya sauko kasa har yanzu muryarsa bata dawo daidai ba ya ce " ina yini Dady Dady bai amsa sa ba ya tsare shi da ido Sudais ya kuma sada kansa ya ce" ka yi hakuri dady, na tuba Dady ya girgiza kai ya ce" bana so irin haka na faruwa da kai dan bana so cutar hawan jini ta kama ka, Sudais ya sauke ajiyar zuciya, ya tabata da yana da hawan jini abinnan ya faru da shi haka a yau da ya mutu Sauke ajiyar zuciya ya yi ya ce" dady, ina so ka yi hakuri yarinyar nan ta tare a cikin satin nan, bana so su yi wani biki wata sabga bana so su yi komai, kawai ta tare Da mamaki dady ke kallon sa, ya ce" aman ai ba haka muka yi da kai ba ko? Da mahaifin yarinyar mun tsayar sai an yi adu.ar arba.in din Marigayiya zata tare, kuma dan me zaka ce kar su yi biki? Cikin kauda kansa ya ce" Dadyna, wannan damar duka a hannunmu take, ni bana so su yi mata komai, indan da hali dady idan har da hali ta tare hakannan. Dady ya dan yi jim, tunani ne ya yi na dan lokaci, tabas ya san mai daki shi ya san inda yake masa yoyo, Sudais ya cika zurfin ciki wai a nan yana fadawa dadynsa wasu sirrikansa ne ma, sannan a duk lokacin da ransa ya baci ya kasance mai yin shiru, baya magana a lokacin, ba yana nufin ya yafe ba, idan yana nigeria damuwarsa ya yi yawa yakan je wajen mahaifinsa domin shi baya takura shi da tambaya a lokacin da ransa ke bace, koda ya huce baya takura shi sai dai ya yi masa nasiha shi ya sa a yau bai tsaya wani abin ba ya nufo wajen mahaifinsa aman har yanzu ya kasa yafe mata wannan abin mai girma wato ta daga hannu ta wanka masa mari a kan gaskiyarsa mari, tambayar kansa yake a kasan zuciyarsa wai ma ya aka yi bai ga zuwanta ba? Aa ya ga zuwanta bari ya yi har ta cin masa, shi yayi wasa har ta kai zuciyarsa mizanin da dan abin haushi ta daga hannunta ta wanka masa mari aman ya kasa daukan mataki mumuna a kanta, aman shi, shi ya san matakin da zai dauka a kanta (😳😳😳😳) Marfin tukunyar ta kumA wurga mata ya sameta a hannunta na hagu ta dafe tana kara sakin yar kara Da gudu mama ta shiga tsakanin su ta ce" Ke Aisha, ya isa haka sai kin kasheta ne a kan da namiji? Yar uwarki ce fa? Ki zo mu je mu nemi malan a san yanda za.a je a bashi hakuri tun kafin wani mumunan hukuncin ya tabata a gare mu, Aisha cikin muryar kuka ta ce" mama, walahi ba yar uwata bace Rauda, kawai ba yar uwata bace, me ruwanta dan ya zage ni? Ai ni ya aibata da rashin tarbiya ba ita ba ko? Mama ki barni da ita a gidannan yau na lalasata, mama ki barni na koya mata hankali domin na lura rashin hankali da kaurin talauci bai ishi kanta ba , banza marar tunani Ni dai ya isa haka dukan, ya isa , ki duba ki ga ko daga saman mashin baki barta ta sauka ba kika wartota kike dukanta, ya isa haka ba zaki hada min zafi uku ba, da me zan ji? Ta juya wajen basma da du jikinta ke ciwo sakamakon dukan da Aisha ta yi mata, dan kuwa ta daketa kamar da wasa ta ce " a kulun fada maki nake ba kowa ya san darajar na gaba da shi ba, ba lale ne ki ce ke dole sai an mutunta maki iyayenki, ke ba karfin da zaki tari abin ne da ke ba, dole a wannan zamanin ka yi hakuri da rayuwa a yanda ta zo maka, haba Rauda haba Raudana Tausayinta ne ya ji ya mugun kama shi, harma ya ji kamar ya juya ya shaidawa Elhaj wannan bukata da wuya ta yiyu , bai taba ganninta cikin rashin tudun dafawa irin na yau ba, Daman zata yi sanyi haka? Cijewa ya yi ya shigo gidan nasa da salama, wanda jin muryarsa ya sa Aisha ta yarda icen dake hannunta ta yi gagawar nutsuwa domin tunda abinnan ya faru wato auren da ya daurawa Rauda take shayinsa, ...... Malan AHMAD KENNAN .. *❣IDAN KA RAINA INDA KAKE❣* Na: *SAJIDA* *_LITATAFAN MARUBUCIYAR_* *_Duk Karyar kada_* *_Yar Mahaukaciya_* *_Neman na kaina_* *_Bani da zabi_* *_Daga tafiya daukar soja_* *_Idan ka raina inda make_* *🌈KAINUWA WRITERS✍🏼 ASSOCIATION*🤝🏻 ```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}``` https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation 2⃣8⃣ *WANNAN PAGE NAKI NE NA SIS LADEEFA ALKHAIRIN ALLAH YA TABATA A GARE KI* kuna da yawa fa, walahi sosai kuna da yawa, na gode da kulawarku jiki yayi sauki alhamdulilah💓💓💓💓💓💓💓 Salamar malan ta saka Mariama juyowa da dan saurinta, ganninsa ya sa ta saki ajiyar zuciya domin ta san dai ko menene malan zai tare mata Kallon su ya yi gaba dayan su , bai ce komai ba ya juya ya shige dakin su Murna fal zuciyar Mariama domin rabonsa da ya shiga dakin su tun ranar da abin ya faru, Hannun Rauda ta kamo ta tsayar da ita kofar dakin ta shiga ciki dan gudun kar Aisha ta kuma dukanta Malan Ina yini Kalonta ya dan yi ya amsa ciki ciki wanda hakan ya sa gwuiwarta ta dan sace Neman guri ya yi ya zauna, ya ce" na dawo kan maganar auren yata , wace na isa da ita Da sauri Nana Mariama ta sada kanta , bata ce komai ba,har ta tuna masa zamanin amarcin su Ya ci gaba da fadin" na yi mata aure sannan mijinta ya shirya tarewarta domin ya ce yana so ta tare karshen satin nan Da sauri ta kalo wajen sa, murya na dan rawa ta ce" malan karshen satinnan fa ka ce? Malan ai mu bamu shirya ba, mai muka ajiye? Mai zamu kai mata kayan daki, kayan kicin, gara? Sannan malan ai bai yi mata kaya ba kamar yanda ake yiwa kowa koda bazawa ce Malan ya ce" haka ne, zancen kaya bai dame ni ba, ya yi bai yi ba tsakannin su ne, aman maganar kaya kin manta ajiyar da nake wajen liman? Duda sun nuna kar a yi mata komai aa, sai nai mata du abinda Allah ya hore min Mariama ta ce" kar a yi mata komai? Me hakan ke nufi malan? Ko mai hali ne mijin nata? Da san mamaki yake kallonta, ya tabata ba dan abin ya bata mamaki bane , bata dai bar maganar mai kudin ba, dan haka ya ce" aure na yiwa yata, ban nema mata mai kudi ba ko marar shi, fatana inda zan kaita ya zamto alkhairi a gare ta, bana son wani taro, idan lokaci ya yi kawai zan kaita da kaina Da mamaki ta bi shi da kallo bayan ya gama ya mike ya shiga canza jalabiyarsa ya dauko wata a cikin jakarsa kano ta yi zahi ya canza ya dauki wanda ya cire da dan klin dinsa ya fice ya barta a gurfane tamkar mai neman gafara Yana fitowa ya ga Rauda tsugune a nan, da yannayin tausayi ya bita da kallo, yana matukar son ya rarasheta aman baya so ta ga fuskar da zatai masa koke koke ko wani abin Kamar da wasa yau alhamis, ya kama sauran kwana uku Rauda ta tare, Malan ya siyo mata gado da armoire mai gida biyu kawai, ya sa akai mata kujerar roba biyu, ya sayo mata kwanon shinkafa bakwai, makaroni leda gom sha uku kaloli, magi kananuwa leda guda, mai littre hudu, su dangin dadawa, kayan yaji, tumatiri da sauransu daidai aljihunsa Sai bayan ya kawo kayan gadon Aisha cike da shakiyanci ta fitar da kudi dubu hamsin ta ce a cikin kudinki na dauki sauran saura wannan Mariama ta karba, bata iya ce mata komai ba domin kwatakwata ta dawo wata so silence, yannayin malan na damunta, ga irin yanda take gannin Rauda, bata cewa kowa komai sai dai ta zauna Daman ita ba wata fitinaniya ba, idan abu ya dameta sosai takan yi ta kuka ne, aman akoy barancin fadin abinda ke cikin zuciyarta....sai dai wannan ba dama, malan ya ki ya saurareta haka ma Mariamar dan kar ta sakota gaba da kuka, aman har.yanzu Mariama a wai take gannin lamarin, aure fa ba wasa ba, danma wulakanci mijin har yanzu bai tako gidan da sunnan gannin matar ba ko gaishe da iyayen Ajiyar zuciya ta sauke, ta je wajen malan da kudin ta mika masa tanai masa bayani Kallonta ya yi ya ce" kirawo min su Zuwa sukai Rauda Da Aisha suka tsuguna bayan sun yi salama Malan ya amsa yana bin su da kallo, RAUDA ta rame, ta rame sosai ana gannin ramarta, ya dan girgiza kai ya ce" wani irin aiki ne kuke haka har aka baku albashi dubun hamsin? Rauda bata iya cewa komai ba sai sada kanta da ta yi, Aisha ta ce" Aba.ai mune masu karamin albashin ma, ai dubu dari da hamsin hamsin ne Ya dago ya kaleta ya ce ya aka yi ya dawo dubu hamsin? Ke kuwa ina naki? Aisha ba tare da wani dar ba, domin ita a ganninta ai hakan ba laifi bane ta ce" kudin makarantar nawa na hada da dubu darin Rauda da darin wajena na kai na zuba, sai ya rage dubu dari shine na raba na bata kasonta ni kuwa na sayo atampopi da mayafai sauran dubu goma sha biyar zan kai dinki Da mamaki.yake kalonta, aa, Aisha wai ko dai bata da hankali basu sani ba suna daukan mumunan halaya ne da ita? Me ke damunta haka? Idan ita batai niyar duba halin da suke ciki ba ai sai ta tausayawa na kanwarta, atampopi, a tunaninsa ta kai wajen da zata yi tunanin daidai da abinda ba daidai ba Wani tausayin Raudar ya kara lulube shi, ya ce" Aisha dauko min atampopin Mikewa ta yi ta je ta kwaso sayayar da ta yowa kanta, ba tare da ta sayo kwarar shinkafa ba, ba damuwarta bane sun ci ko basu ci ba ita dai ta san du rintsi dole mahaifin su ya basu koda garin kwaki ne, idan kuwa cikinta ya dauka koda me ta ci bata da damuwa ita dai damuwarta ta saka mai kyau a yi cudanya da ita cikin yayan manya Dadaga atamfofin ya yi, wajen kala goma sha daya ne manya guda takwas sai kananu guda uku, Cikin nutsuwa ya kasa biyu, dayar da ta hayo ya ware gefe, ya dauki mayafan ya kasa suma biyu wato hudu hudu Da kansa ya zabarwa Rauda kashi gudan ya turawa Aisha guda wace ta yi kasakai tana jiran karin bayani Gannin bai ce da ita komai ba ya sa ta ce" Aba, kayana ne fa? Idannuwansa ya dago a hade, ya ce" Eh sai na raba maku da kanwarki ba, ai kudinta naki ne, abinta naki ne kamar yanda yake naki nata ne Ranta a matukar bace ta mike ta bar kayan a nan ta shige wajen mamansu ta fashe mata da kuka tana fada mata wai Aba ne ya kwace mata kayanta ya baiwa Rauda bayan ita an yi mata aure ko yaya dai mijinta ai zai yi mata sutura komin talaucinsa Muryar Malan ce ta katse ta ya ce" Aisha, Aisha, ina miki tsoron rayuwa, ke ko kunya bakya ji? Kin kama kudinta kin kashe ke mai son kanki dan na raba abinda kika sayo shine zaki zo kina daga murya? Aisha kayan nan gaba daya ba zaki saka ba sai ki je gidan da kika san za.a hukunta ni ki fada, kuma wannnan dubu hamsin din zan mayar da gadon nan daman dubu ashirin na sayo mata shi sai na cika gaba daya a bata na gani na fada ke kuwa mu zuba ni da ke da du wanda ya daure maki! Yana gama fada ya fice ya bar Mariama da sakin baki tana mamakin su malan harda habaici aka koya? Shi dai bai mata kirikirin da ita yake ba aman kuma bai boye nufinsa ba, Aisha kuwa kara volume din kukanta ta yi tana rantse rantsen idan ya dawo da dinkunnan sai ta kwashe abinta ai ita ta yi aikinta ba wani ba Ranar asabar mota yar kurkura ta kwashi kayan Rauda aka loda ta kai ta dawo ta kuma kwasa an yi kaiwa uku kafin ake kwashe komai, direban nan dai kurmanta ya yi jigilar nan, yana gamawa ya dawo ya kai Mariama ita da Aisha dan gyarawa Rauda daki bisa umarnin Malan ELHAJ SUDAIS kennan, dan karamin gidan Samir ya sa samir ya kama masa, daki biyu ne kwal, da bayi a cikin kowani daki sannan dakunnan ba wasu tafka tafka bane, Tsakar dakin da dan fadin sa sai kicin a tsakar gidan Hankalin Mariama ne ya dan kwonta, duda bata so yarta ta auri mai dan hali ba aman irin wannan ginnin ma ba kowa ke samu ba, dan kuwa ya isheka zaman duniya Aisha kuwa dariya ta ringa yi ta ce" mama, wannan gidan da gidan mu mai ya raba su? Abinda ya raba kawai gidan mu ginnin laka ne wannan kuwa na suminti ne aman kin ga gida kukub shima tamkar akurkuki? Kai Allah kai damo ga harawa mama, aurena da Elhaj ya tabata zaku sha kallo, yan uwanki sai sun dawo suna baki hakuri dan su sami wajen zama Mariama ta yi murmushi ta ce" Allah yarda Aishana Aisha dake buga labule da kusa ta ce" yama yarda tunda ya kaini aiki kampaninsa Mama ta ce" aa, wai kin tabata ba za.a kore ku a ma.aikatar nan ba kuwa? Aisha ta ce" ai ba ni na mare shi ba, Rauda ce, sai na fada masa ya yiwa girman Allah ya barni na yi aikina wace ta yi masa wannan aikin an yi mata auren dole an hadata da talaka irintA! Mariama ta dan girgiza kai ta ce" da alama halayenki daya da aunty , yanda kike kin jinnin talaka tamkar ita ta haife ki, ni kuwa soyaya bata barni na ga aibun abanku ba a lokacin Aisha ta sauko ta kamawa Mariama shinfida tabarmar ledar ta ce" hum Mama, ai walahi ba zan boye maki ba kin cuce mu! Da kika auri aba, ni fa kunya nake ji a nuna shi a matsayin mahaifina, kaf anguwar mu mune karshen talakawa shi yasa ko zaka aka fitar sai dai ki ga yayan manyan nan sun kwala salama daga kofa an miko mana zaka, ga nakasasu ko? Wa.inda basu da komai.... Mariama ta girgiza kai ta ce" aa kar ki ce haka, kowa da irin destin dinsa Aisha Destin? Mama destin, ai mutun na iya juya destin dinsa ya dawo masa yanda yake son ganninsa Mariama ta ce" lalalalla, ko daya, rubutu ne Aisha, du yanda Allah ya tsara maka haka yake zuwar maka, a gaskiya bana fatan irin rayuwar babun da nayi yayana m su yi, ina muku adu.ar samun nutsuwar rayuwa, shi kuwa farin ciki konciyar hankali shi ne gaba da komai Aisha da ta ajiye kujeru hudu , kennan an saka labulaye an sa kujeru, an sa dan prm mai sunnan Allah guda biyu, sai tulu daga can gefe dakin ya gama haduwa da iya abubuwan nan ta shiga tsakiya ta nunawa mahaifiyarta ta ce" mama , farin ciki? Konciyar hankali a nan? A nan ai ba konciyar hankali, ba maganar wasa da dariya, ba maganar samun nutsuwa, talauci? Ai talauci bai yi ba, baki ga yanda talaka ke bacin rai ba? Ai yanda aljihunsa yake ba annuri haka zuciyarsa take, mama, ke dai kawai a yi rayuwa aman ni? Ba zan auri talaka ba! Girgiza kai Mariama ta yi, ta lura in dai kan wannan maganar ne Aisha ba zata taba sauraronta ba dan haba kawai sai ta yi gaba ta kyaleta, ita kam dakin Rauda ba laifi, daidai talaucin su sun yi kokari sannan gadonta an samu da setinsa komai ya yi kyau sosai Haka suka gama suka share ko.ina suka kara wanke bayin suka fice Ba kunshi, ba kitso Rauda? Ban ji kina neman mai kunshi ba yar gidan Abanta Malan ne ke tambayar rauda da yama bayan ya dawo ya tarda ita ta yi wujiga wujiga da ita sai kallon waje guda, Murya a raunane ta dago ta kali Abanta ta ce" Abana, ka yafe min Abana Sai hawaye sharsharshar Waje ya samu ya zauna kusa da ita , a hankali ya kamo hannayenta biyu hakan ya sa ya ji jikinta zafi rau, Zuciyarsa ce ta karaya, ya ji idannuwansa sun cika da hawaye, murya da alamar rarashi ya ce" kin kasance mai yi min biyaya, kin kasance mai yi min godiya a dukan abinda Allah ya nufe ni da samu kin kasance mai karfafa min gwuiwa, LALLA RAUDA albarka ita ce a kulun nake saka maki, Rauda ba zaki wulakanta a duniya ba, ki kadara komai ya same ki rubutacen al.amari ne ba wanda ya isa ya ja da hakan! Ki kontar da hankalin ki, na san rashin gannin wanda na aura maki na damun ki da rashin sannin ko waye, mahaifinsa ya gabatar da maganar ya zo ku gana sai dai wata fitina da ta bilo a nan gidan wace sai bayan daurin auren nan na fahimci komai ya sa na kiyewa maganar zuwansa, sunnan mijin ki *SUDAIS MUHAMMAD* Dumdum ta ji gabanta ya fadi aman kuma sunnan yayi mata taushi a harshenta, sai ta tsinci kanta da maimaita sunnan a kasan zuciyarta tana mai adu.ar Allah ya sa mai tausayi ne Malan ya ci gaba da fadin" kar ki yarda rudin duniya da mugayan mashawarta su saka ki canza halayen ki na kirki, ki kasance mai yawan adu.a da hakuri sannan ki yi masa biyaya, na tabata koda da wata manufa ya karbi auren ki Allah zai hana shi wulakanta ki A gaskiya ta ji maganar mahaifinta ta sanyaya mata zuciya, ta ji zuciyarta ta samu nutsuwa, a hankali ta dora kanta saman hannunsa daidai nan mai kunshin da Aisha ta je nema ta shigo Lale ta zanawa Rauda dan kadan, bashi da wani yawa ta kuma zanawa Aisha kafa da hannu itama kuma jan lale ne yayi masu kyau sosai Malan dake zaune saman tabarma , sosai fuskarsa take cikin annuri ya kali Mariama ya ce" Mariam Da dan sauri ta kalo wajen sa, rabonsa da ya kirayeta da sunnan nan har ta manta, Kalonsa ta yi sosai ta amsa tana rike da hannun Rauda guda dan kar na yatsutsan su hade, Malan ya dan yi murmushi ya ce" kema a zana maki mana kunshin Da mai kunshi da Rauda suka sa yar dariya, somin yanda Malan ya yi maganar abin sai ya mugun baka dariya, haka Rauda ta ji zuciyarta wasai domin Mariama ma biye masa ta yi ta mika hannunta bayan an gama yiwa Aisha aka zana mata Mai kunshin dai itama ba wata mai shi din bace, malan ya zare har dari bakwai ya bata ta tafi tana ta godiya Ba yanda Mariama batai ba dan Malan ya amince a dan yi taro aman ya kiya, Rauda kam ta dawo kuma sai ido, gashinta batai masa komai ba kiyawa ta yi a yi mata kitso sai kawai dan shirye shirye da ake yi a cikin gidaan nasu Da kyar Mariama ta roki malan ya baiwa Aisha 2 complet a cikin kayan nan aman ta ki karba dan haka da haushi ya karbe ya hadewa Rauda a sabuwar jakarta kano ta yi zahi, dinkunnan kuwa sun mugu mugun yin kyau domin telan yan mata ya kaiwa ya bashi abinda gare shi shi kuwa ya yi mata dinkunna ba laifi Rana bata karya sai dai uwar diya ta ji kunya, Ranar lahadi ranar *tarewar Rauda* ...........mu je zuwa...... *❣IDAN KA RAINA INDA KAKE❣* Na: *SAJIDA* *_LITATAFAN MARUBUCIYAR_* *_Duk Karyar kada_* *_Yar Mahaukaciya_* *_Neman na kaina_* *_Bani da zabi_* *_Daga tafiya daukar soja_* *_Idan ka raina inda make_* *🌈KAINUWA WRITERS✍🏼 ASSOCIATION*🤝🏻 ```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}``` https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation 2⃣9⃣ A yau ranar lahadi, yau ne ranar tarewar Rauda Tunda safe take konce a dakin su, ta yi shiru ta afka tunani..... a zuciyarta sai kokowa take da tunanin kwakwaluwarta fadi take" Aure ne aka yi min, tunda aka aura min mutumin ban taba ganninsa ba , shima hakanan duba da wasikarsa ta farko, Ban san halayarsa ba sai sunnansa kawai da Aba ya fada min , *SUDAIS* wanene kai? Shin bawa ne mai son kusanci da Allah mai burin tashi a kusa da ma.aikin Allah salalahu alaihi wa salam, mai son tashi ne babu shanyayen jiki? Shin ka kasance mai aure aure ne ya sa ka karbi aurena ba tare da ka yi tunanin komai ba irin ni wacece, halaya na, tarbiyana, mai tausayi ce, na iya tatalin rayuwa? Sai kawai ka aure ni........ SUDAIS ni dai *BANI DA ZABI* a yanda rayuwa na zata kasance.. SUDAIS ina fata ka zamto min *ZABIN ALLAH* Muryar Sarah ne ta karade gidan tana rafka salama daga bakin kofa Da murnarta Mariama ta fito ta saka sabuwar atamparta ta tarbi auntynta Kallon sama da kasa take binta da shi, Sarah kuwa ta dare saman kujerar malan ta roba ta dage kafafuwanta sai yatsina fuska take dan har cikin zuciyarta kyankyamin yan uwan momynta take Aisha ce ta gaishe su itama ta zauna tana sauraron yanda mamanta ke baiwa yar uwarta labarin yanda auren ya kasance Aunty ta ce" lalle kin bari Ahmad ya ga damarki fiye da tunnanin mu, yanzu in ba wulakanci ba daga wannan yar maganar shikenan sai cibi ya zama kari? Daman da niyarsa in kin ga haka Mariam, mai yiwuwa mutumen mai abin hannunsa ne Aisha ta yi carab ta ce" aa aa, talaka ne tukuf, talaka ne na sosai baki ga yanda gidan da ya kama mata yake ba kuma da ganni ba malakinsa bane gidan haya ne Sarah ta yi wata irin dariya ta ce" ba dole ba, ai sai takama da kyau ita bata gannin talaucin dake gidinta sai shegen girman kai tana dadagawa mutane kafada wancen lokacin kinga yanda take hararan mom dan ta fadi mahaifinku talaka ne? Ita fa bata zuwa gidanmu ko da aike wai ita mai son uba kar a zagar mata ubanta Aisha ma dariyar ta yi ta ce" kai , ai ba.a kwana biyu bata sha marin mama ba, dan kuwa daga an aibata aba shikennan sai ta buga ta tare Sarah ta yatsina fuska ta ce" sai kace wani mai biya mata bukatunta na yau da kulun, ni dai da ace Mom ta auri talaka da ta janyowa kanta masifa wly, Aisha ta yatsina fuska ta ce " haka dole muke zaune, aman ni wly idan abana talaka ne ba zan auri talaka ba, yanzu haka tana ji tana gani za.a kaita kamar wani auren tsohuwar bazawara marar galihu ko dan taro baza.a yi ba Rauda dake daki tana jin du abinda suke fada ta kara gyara konciyarta tana tir da wannan halaya nasu, su nan har sun sami abin jifanta da shi, ai ita alhamdulilah an ga nata auren su su kuka da kansu ba burin zabo mai kudin ba duniyar nan da ta rikice haka sai a slow Zaman Mariama da aunty a wunin nan ba wani zaman an zo tayata murna bane, zama ne ta yi ko ruwan gidan bata sha ba sannan ta wuni ne tana yi mata gore gore da abubuwa dai mararsa dadi hakan ya sa ta kara tsurewa du ta shiga tunanin rayuwar da Raudanta zata je ta yi Da yama sukai tafiyarsu bayan aminci ya kulu tsakanin AISHA da Sarah abinka da halaya daya Bayan salar magarib, Aba ya fito tsakar gida ya tarar da yayansa da matarsa suna zaune sun yi jigum jigum suna jiran dawowarsa daga masalaci domin ya fada cewar da ya dawo za.a tafi Daidai wannan lokacin baraka makociyar su ta kawo turaran wuta da humarar da mama ta bada dubu guda da dari uku aka kawowa Rauda, Mama ta karba ta saka a jakar Rauda tana yiwa Baraka godiya wace ta bisu da kallo tsegumi cike da cikinta wai an yiwa Rauda Aure, wa ya aureta? A ina aka daura auren? Ya aka yi basu yi taron tarewarta ba ? Duda akoy halin babu a tare da su aman babun bata kai nan ba gaskiya haka dai ta juya ta tafi ba dan ta so ba sai dan bata samu fuskar tambaya ba Malan ya shigo, sabuwar doguwar fara jalabiya ce a jikinsa, ya kafa hularsa harda turare ya fesa masha Allah malan ya fito das da shi Da kallo ya bi su inda ya tsayar da kallon sa kan Rauda, Bakin dogon hijabi ne ta dora kan riga da zaninta na atampa, ba walwala ko daya a tare da ita sai ma lagadab da ta yi Dan girgiza kansa ya yi ya dauki babar jakarta ya fita ya dawo ya dauki kondon kayan sabulunta da kayan kwaliyar da ya dan tsintsinto mata ya kai ya dawo Shi kam bai san mai zai fada masu ba, ya yi mata nasiha a jiya har shiga baci yanai mata nasiha dan haka ya umarceta da ta mike su tafi Gabanta ne ya fadi, zuciyarta ta karye, ta mike a hankali ta dan fara takawa Mariama dake tsaye ta rungume hannunta na dama saman kirjinta, ta bi yarta da kallo, Ji ta yi wanni irin kuka ya zo mata wanda ta kasa rike shi Tun karfinta ta sake shi ta furta sunnan RAUDA da dan karfin da ya sa Rauda ta tsaya cak daidai kofa kusan Abanta Da sauri mariama ta karasa ta rungume Rauda a jikinta wace itama ta saki kukan zuciyarta na tsale tana jin kamar ta shige cikin mamanta ta huta da wannan tashin hankalin Murya a raunane Mariama ke san bubuga bayan Rauda ta ce" its ohk Lallana, kin san me na tabata ba zaki sha wahalar rayuwa ba domin kin kasance mai biyaya Kina iya kokarinki dan gannin kin fita hakina ni magaifiyar ki, kin fita hakin mahaifin ki, sai na yar uwarki, Rauda ina sane da dukan abinda ke faruwa, ina sane da dumbin hakurin da kikai , Wannan aure da yardar Allah sai ya zame maki alkhairi, ki yi hakuri da jarabawar rayuwa kowa da irin tasa, kuma indai bawa ya cika mai imani sai Allah ya jarabce shi Ajiyar zuciya Malan ya sauke yana kallon Mariama, ya ji dadin kalamanta wa Rauda, a kasan zuciyarsa ya furta" Mariamana kennan mai hali kala daban daban , wataran ta yi halaya mai kyau da nagarta wataran kuwa ta tsula tsiya😁 Haka ta rako Rauda har bakin mota, Mota ce baka yar madaidaiciya da direba kurma a ciki Haka suka shiga suka dauki hanya wanda suna tafe Aba na kara yi mata nasiha kasa kasa Suna karasowa kofar gidan Aba ya ce" yaro makulin gidan a wajenka ne? Kurman direba ya dan juyo saitin Aba ya ce" Aa Aba ai an zo an bude gidan an kuna inji Da mugun mamaki take kallon sa harda sakin baki ta ce" kai Aba daman wannan yana magana? Aba ya amsata da Eh man Rauda Da mamaki ta fito hannunta cikin na abanta tana kara kallon direban da ya sada kansa kasa yana jin faduwar gaba da dana sannin amsa aba da ya yi a kusa da Hajia Har ciki Aba ya kai Rauda bayan ya kawo mata kayanta ya saka ta yi adu.o.i shima ya yi mata ya mike da niyar tafiya Da kyar ya samu ya rabu da ita, ita tana kuka shima yana share hawaye ya tafi ya barta a falonta dan madaidaici an kuna inji fitilu a kune na daki daya da na bayi da na falo da tsakar gida Ta jima zaune tana kuka, a hankali ta mike ta nufi dakin mai fitila a kune ta yi adu.a ta shiga, nan ta ga kayanta gadonta da sauransu sannan harda bayi Bata iya komai ba sai dakin da ta janyo ta rufe ta yi konciyarta a nan saman dan bed dinta ta rufe ido sai tunani Kamshi yake bazawa, hannunsa rike da leda mai tambarin gidan suya, a yau da yake cikin farin farin ciki na karin kusantuwar marar tarbiyar matarsa sannan abin son zuciyarsa dole ya ci kazar kampanin suya Saman doguwar kujera ya tarar da ita, ta cakare ta saka suturar siri a jikinta Man bleating din yayi mata yawa ya sa har ana gannin jijiyoyi tsanwaye a jikinta , Ajiyar zuciya ya sauke ya nufi dakinsa Da sauri ta ajiye whatsup din ta bi bayansa ta tarar ya zauna ya bude ledar da ya shigo da ita ya ciro takardu ya bude ya maida hankali ya fizga ya kai bakinsa Da fara.a ta matso jikinsa ta dora kanta saman kafadarsa, murya kasa kasa ta ce" Uban masu gida, na daina shafa man fa Murya ciki ciki ya amsata da " kin taimaki kanki Lumshe idannuwanta ta yi, a hankali ta saka hannunta cikin sumar kansa ta shiga dan shafawa tana yi masa tafiyar tsutsa Da gaya gaya ta ringa tsokalo shi, tana kokarin sai ta kai shi bango A hankali ya fara hawa caji, sai dai yana lumshe idannuwansa hoton marin Rauda ya shigo idannuwansa wanda ya ji tassss din har kwakwaluwarsa Da sauri ya bude idannuwansa da mugun firgita sannan ya rike hannun Humaira gam wanda har ya saka ta saki dan kara Saurin cika mata hannun ya yi yana mikar da ita, fuskarta ya kafe da ido a zuciyarsa yake fadin" so nake na muzanta mata, na wulakantata, na yi mata abinda gabannan ba namiji ba ko mace yar uwarta zata ji tsoron kai hannunta yatsar kafarsa bama fuskarsa ba, Heartbeat koda kece lumfashina sai na koya maki hankali, sannan idan halaya mamanki kikai na son abin duniya da wulakanta mutane sai na cire maki su, sai kin zama yanda nake so kafin na nuna maki how na mace a kanki, karya kike Heartbeat soyayar ki bata isa ta saka na zama banza namiji ba, wly sai na koya maki hankali .........😟😟😟😟 A wannan ranar Humaira ta ji jiki ba na wasa ba, domin kwanakin da ya diba sai da ya sauke mata a kanta waima dan sama sama yake mu.amula da ita sanadiyar warin da take fitarwa na man bleating da ya cinye mata fata Da safe du irin wahaluwar wannan da ta yi ki ta yi ta shiga ruwan zafi dan gudun kar fatar ta ta jimu warkewar ya zama aiki, haka ya barta ya shirya ya dauki ky din kotarsa ya yi fitar sirri da safiyar nan ( 🤔, ko baka daina dan Allah ba ai sai ka daina dan lafiyar jikinka 🤣) Rauda haka ta kwana ido bude domin rabin kwanan ta yi tana tunani daga baya ta waye kan darduma tana ta kaiwa Allah kukanta, Tsoro, mamaki, fargaba, tashin hankali sun yi mata yawa, kanta ba zai dauka ba, ita dai kan jiya zuwa yau bata ji motsi ba sannan bata ga shigowar mutun ba, mai hakan ke nufi? Yar karamar wayarta ta duba ta ga karfe bakwai ta dan gita, Tunda ya shigo anguwar ya shiga da ya sannin sakawa a kawota anguwar nan da farar safiya aman du an cika anguwar ana ta kakayatu, rabonsa da irin wannan rayuwar tun zaman tasha na dan watani lokacin yana harkar waya Kofar gidan ya parka , ya kurawa kofar ido Kansa ya dafe ya dauki wayarsa ya danawa samir kira Samir dake barcin safe monday ya ji wayarsa na shaida masa kira na shigowa na ogansa Ai wata irin tima ya yi ya dauki wayar yana amsawa Run kafin ya kai gaisuwarsa Sudais ya ce" SAMIR aman ka gama raina min wayo, dan nacee ka samo karamin gida ne zaka saka min *MATA* a wannan gidan? Me ta yi maka da zafi haka? Ni *MATA* ta shiga nan ina raye? Samir kamar yanda tarihinta ya bambanta a rayuwana, ta zama ta farko da ta kafa baban tarihi a rayuwana haka dole komanta ya zama daban, tabas ina so na ganta a gidan da bai kai wanda na tanadar mata idan na huce ba aman kuma ba irin wannan gidan ba SAMIR! Baki na rawa Samir ya ce" am, am, oga ka yi hakuri...abanta kuwa baka ga yanda ya yi murna ba sannan ya ce zai zuba mata abubuwan da ya yi mata kar mu saka komai Sudais ya ja tsaki ya kashe kiran ya fita a motar ya nufi gidan Du takunsa daya sai gabansa ya yanke ya fadi, har ya shigo falon Idannuwansa ya kwalalo gannin irin shirin fallon, murmushi ya saki a ransa ya furta" daman akoy mutanen da kwadayi bai yi masu kanta ba du irin kangin da suke ciki irin Aba har yanzu??? Juyawa ya yi wajen tableau dake kafe mai sunnan Allahu hakan ya sa ya baiwa kofarta baya Tunda ta ji alamar motsi ta mike ta fito a hankali dan gannin ko waye???? Tana fitowa ta hangi bayan mutun, a tsaye zambal da shi, sannan da gashin kansa luwaiwai sai sheki yake, bayan kwabrin hannayensa dake waje fari tastas ga cika da jijiyoyin wajen sun tsatsaya kyam, Kafarsa cikin bakin takalmi sau ciki take, fallon gaba daya ya cika da kamshi Wannan kamshin ta san shi, wannan kamshin hancinta ya saba shakar sa, aman a ina? A ina ta san kamshin nan? Gabanta ne ya mugun faduwa wanda har sai da ta ji zata zube dan razanar da ta yi Murya na rawa ta ce" mamamalan wanene??? Shima sai da ya ji gaban nasa ya fadi, girar sama da ta kasa ya hade, a hankali ya shiga juyowa wanda hakan ya bata damar gannin........... *❣IDAN KA RAINA INDA KAKE❣* Na: *SAJIDA* *_LITATAFAN MARUBUCIYAR_* *_Duk Karyar kada_* *_Yar Mahaukaciya_* *_Neman na kaina_* *_Bani da zabi_* *_Daga tafiya daukar soja_* *_Idan ka raina inda make_* *🌈KAINUWA WRITERS✍🏼 ASSOCIATION*🤝🏻 ```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}``` https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation 3⃣0⃣ *CIGIYA, INA CIGIYAR NOVEL DINA BANI DA ZABI DAGA 1 HAR 42 PLEASE, NA SO TSAYAR DA SHI AMAN SISINA TA RIKICE.MIN DA RIGIMAR SAI NA KARA MATA WATO SAI NA SHIGA SOSAI, DAN ALLAH DU WACE TAKE DA TA TURON TA WANNAN NUMBER 91466605 NA GODE SAJIDA CE* Hakan ya bata damar gannin fuskar mutumin da ya shigo mata gida da sasafe wanda idan an barta zata iya cewa mijinta ne ko wani makusancinsa Tashin hankali wanda ba.a saka masa rana, idannuwanta gaba daya ta kwalalo waje, carbin dake hannunta fari dan karami ta saki bayan cikin lazumi take A lokaci daya jikinta ya dauki rawa, rawa na tashin hankali, kafafuwanta suke neman zubar da ita kasa , Dan yatsanta na dama take kokarin tsayarwa a daidai inda yake aman sai rawa yake ya kasa tsayawa Sudais dake tsaye sai ka rantse bai san ba wani abu wai shi sakin fuska ko fara.a a rayuwa, tsaye yake tamkar gunki tamkar zai yi arangama da mai bashi sakon mutuwarsa aman a kasan zuciyarsa fada yake da zuciyarsa wanda har zufa ta dan karyo masa ta wahala, kokowa take, luguden daka take tana hantsila tana kukan sai ya barta ta kawo ga abincinta, mai saka ta dokawa tun ranar da ta aminta da ita, so take ya je da gudu ya rungume yarinyar dake tsaye a gabansa ya rukunkumeta ya kankangeta ya dabaibayeta ya lasance koda lumfashi zata shaka sai ya biyo ta bakinsa ya shiga huhunsa ya janyo da hancinsa ya mika mata, kallon fuskarta yake ta yi fayau da ita, gurbin idannuwanta sun yi jajir tamkar wace take cikin jinya, lebenta kalar ash color sai rawa yake na sama da na kasa da abin dan yawu da ya jike shi sharkaf ya saka yake kyali tamkar ya cafke shi ya tsotse shi har sai ya cinye shi a bakinsa Aman wani gefe na zuciyarsa ke yiwa sauran fada cewa" ita ce fa, ita ce ta daga hannunta na dama ta wanka maka mari a gefen fuskarka na hagu mai cike da yalwatacen saje da dumi na fata da cika ido dan kawai ka yi magana kan gaskiyarka, ita ce fa bayan ta wanka maka mari a bainar jama.a ta biyo la da nuna yatsa wanda a yanzu ma take nuna maka dan yatsanta karami mai dogon farce fari mai kyali, ita ce ta kafa tarihi a rayuwarka, abinda ba.a tabai maka ba ta kwana lafiya.....tabas kana sonta sudais, sai dai hakan ba zai saka ka nuna mata tun yanzu ba Shima idannuwansa ya zaro, irin abu ya dake shin nan ya nuno ta da yatsarsa ya ce" you? Me kike a nan? Kara zaro idannuwanta ta yi gabanta na ci gaba da dukan tara tara, muryarta na rawa ta ce" aaaaa, ai nan nan gidannn,,.....gidan wanda ke aurena ne Bai bari ta kai aya ba ya ce" what?, ke? Kina nufin ke? No ba xai yiwu ba, ba zai taba yiwuwa ba, ke ki fitar min da matar gidan tun kafin laifukanki su fi karfin girman kanki Da sauri ta kankame hannayenta biyu a kirjinta, ta dan dago da fuskarta ta kallo fuskarsa wace ta saka a take ta ji kamar ta fara zubar da jinin haila ( fargaba idan ta yi yawa tana takalo jinnin haila 😁🤦‍♀ ) Fuskarsa ta mugu mugun tsoratar da ita, sai a yau ma ta shiga tunanin abinda ta aikata, yanzu wannan fuskar ta mara da hannunta? Ita Rauda? Innalilahi wa.ina ilaihi raj.une kawai take ambata a cikin zuciyarta sannan a hankali ta sulale kasa still hannayenta a samankirjinta tana ta rawar jikin da tamkar an jona mata wayar wuta Cikin dan daga murya da muryar nan tasa mai abin tsoro ya ce" wai ba ke nake jira ki hiwa matar gidan magana ba? Ke ko danginta ce ke sai na yi mata abinda bata taba tunani ba sanadiyar ki , sannan ki daina tsare ni da idannuwan nan naki suna saka na ji tamkar na shake ki na huta! Karin firgici da tsoro ne ya saka Rauda dora hannunta a saman kanta, kuka ne ya kubce mata mai karfi tana girgiza kanta irin tana cewa aan nan, Zuciyarsa ya kai nesa domin wani irin tsale ta yi masa na ya je ya lalashi abincinta, kokari ya yi ya karasa sosai kusa da ita wanda gannin ya karaso ya saka ta mike da sauri ta juya da niyar fadawa dakinta ta rufe sai dai ta makaro domin rikon barawo a hannun yan sanda ya yi mata ya juyota da karfin tsiya wanda ya saka ta daki bangon dakin ta yi tagataga da kyar ta samu ta rike kanta ta ja ta tsaya jikinta na rawa hawayenta na tsannanta gudu , Murya a dake SUDAIS ya ce" i said ina *MATAR SADAKA* ne? Jin kalamansa take tamkar saukar aradu, a fili wannan karin ta furta tun karfinta" innalilahi wa.ina ilaihi raj.une, ya Allah ka farkar da ni a mafarkin nan, ka tashe a mafarkin nan, Da sauri ta kalo wajensa bata damu da yanda kafarta ta farai mata zogi ba ta ce" kana nufin kai ne? Kai ne? Tsareta ya yi da mayatatun idannuwansa ya ce" ni ne wa? Murya na rawa ta ce" nonononono ba haka bane, ni na san ba haka bane, domin abin bai hadu ba ko daya, ka nemo inda nake ne ka biyo ni dan ka rama abinda na yi maka? Ka ga ka fita a gidan nan tun kafin ka jaza min fitina, na yi maka abin nan ne ranar dan ka daina wulakanta matar da ta mace a kaunarka, dan ka daina zagin mahaifan mu , idan kuwa baka yafe min ba ga fuskana ka rama dan Allah Gefen fuskar nata yake kallo da mugun bege wanda a fuskarsa kuwa ya nuna tsantsar kyama, zuciyarsa ke fadin" ka dan shafa fuskar mana ,? Wata kuwa fadi take kai ka nuna mata kai namiji ne ka wanka mata marin da sai ta suma dan azabar zafi Har ya daga hannunsa da tarin mugunta sai zuciyar soyayar Rauda ta rinjayi mai kin ta, da sauri ya sauke hannun nasa ya zubawa girar idannuwanta ido wada ta rufe idon ruf, du hawaye ya jiketa ta dan harhade da junnanta aman a tsaye kyam, hijabinta baki ne dai a jikinta tamkar mai takaba Murya a dake ya ce" ke wai zaki bani amsa ne ko sai na hasala? Rauda ta ce" na tambaye ka sire, na kasa gane inda ka nufa Kai tsaye ya amsata da " ina nufin matar da aka bani a masalaci Maganarsa ta yi daidai da tsinkewar tunaninta, dago da idannuwanta ta yi ta sauke su a cikin nasa kyam wanda bata ma san ta yi ba, me yake nufi? Yana nufin ita Rauda ita ce aba ya bashi a matsayin mata ba Aisha ba? Ta ya haka ta faru? Aman daman mai aure aure ne ko me? Ya aka yi sallah ta kama shi a masalacin anguwarmu a wannan ranar? Ai kafin wannan abin ya shiga tsakaninmu ne, wannan wata irin kadara ce? Wannan wani irin tashin hankali ne ke tunkaro rayuwarta da gidan su? Su kennan Haka za suna rayuwa jarabawa Kala daban daban? Ya salam ya zata yi me zata yi? Indai wannan bawan Allahn dake gabanta a tsaye wanda ta daga hannunta ta sharara masa mari, wanda yayarta ke haukar so har take ikirarin du wace ta gita ta gabansa sai ta halakata, bama wannan ba, wannan mutumen mai shegen kyau cika arziki mulki ai ya fi karfin tunaninta, aman kai da ayar tambaya a lamarin nan, wannan fa shine ake kira da *UBAN MASU GIDA* me gidan nan ke nufi? Aa ya shiga rudu ne, tabas a cikin rudu yake, in kuwa ba haka ba ne fa? In fa shi ne aka aura mata ? Da sauri ta girgiza kanta tamkar zarara ta furta a fili wanda bata yi tunanin ya fito ba cewar" aa, bama zai taba yiwuwa ba, sam hakan ba mai yiwuwa bane, ,ba zan taba rayuwar aure da mutumin da auntyna ke so, na tabata ma ba shi bane ba zai taba zama shi ba Sudais ji yayi sam bai ji dadin maganarta ba, daman ya ji tsoron kar a je ta yi masa irin haka, wato yarinta na damunta ai sai ya ganni Kina nufin ke, kece dad ya auro min? Ya Allah why m? Kasa ta yi saman gwuiwoyinta, gaba daya ta yi sanyi sai dumbin tashin hankalin da take ji, kafafuwanda dake cikin takalmi sau ciki ta tsurawa ido, ta tuno fitinar Aisha, ta hango gidan su da kalar matarsa, karyar da kai ta yi ta ce" ka yi min rai ka sawake min aurenka a kaina, ba zan iya rayuwar aure da kai ba, soyaya ba zata taba shiga tsakaninmu ba, ba farin ciki a tarayar mu, kA yi min rai ka sawake min kar rigimar da ta tunkaro ni ta shafe babina Kowace kalmar dake fitowa daga bakin lalla tana shiga kunen sudais ne da kibiya mai mugun tsini tana kaiwa zuciyarsa farmaki, Idannuwansa ya rintse jin yanda zuciyarsa ke hawaye mai zafi, Da sauri ya juya ya fice ba tare da ya tankata ba Har ya kama kofar ya juyo da mugun sauri ya karaso inda take, Hannunsa na dama ya saka ya damki damtsanta na hagu ya duka yanda take iya jiyo numfashin sa da hucin da yake fitarwa, idannuwansa ya saka cikin nata ya ce" *ke, ban aure ki ba dan soyaya! Na je sallah na ji tausayin tsoho mai daraja! Ki sani da na san ke ce da ba zan taba aurenki ba domin bana ra.ayin mata masu furtawa namiji kalmar so tun kafin ya taya, abinda yayarki ta aikata zaki aikata ne domin uwar rainon daya ce! Na fada uwar rainon daya ce! Ki kiyayi furtan munanan kalamai domin ba zaki ga da kyai ba! Ki shirya karbar hukuncin marin da kika buda kazaman hannayen ki kika yi min! Dole ma na rike ki na wani lokaci ko dan na koya maki hankali!* Yana gama fada ya cika mata hannun da ta ji ya sangaye ya juya ya fice tamkar zai tashi sama Da kallo ta bi shi ta sume a zaune, mugun tsoro ya hannata kukanma , haka ta zauna ta tsurawa kofar ido Shi da zai nufi ma.aikata direct gidansu ya nufa Ta babar kofa ya shigo ya tsayar da motar a wajen da ba na parking ba ya shige direct bangaren hajia kaka domin ya san suna can warhaka Tunda ya shigo da salamar da iya shi ya san ya yi a lebensa suka tsura masa ido suka tsayar da hirar fa suke Hafsat! Ya fada da kakausar muryar sa Da sauri ta kallo wajensa ta mike tana amsawa cike da nutauwa domin baya kiran sunnanta gatsau haka sai da dalili Bai baiwa kowa fuskar musu ko wani tambaye tambaye ba ya ce" ki mike ki dauki kayanki, ke da Humaira direba ya kai ku sabon gida Yana gama fadar haka ya juya tamkar zai tashi ya fice ya yi bangaren su inda suka raka shi da kallo Hajia kaka ce ta ce" lahaula wala kuwata yau na zo zamani da uwa ke tsoron danta A tare suka juyo da Momy, Hafsat da Humaira wa.inda suka mike cikin gagawa dan bin umarninsa Momy ta ce" hajia wani irin tsoro kuma? Hajia kaka ta karkace baki ta ce" eh man, tsoron Sudais kike, yaushe zai shigo mana zikau ba salama ba gaisuwa ba ya kuke ya bamu umarni kuma a mike ana zanzana a je a aikata Hafsat ta saki yar dariya tana kallon hajia kaka ta ce" to ke mai ya hana ki yi masa tsawa kakus? Hajia kaka ta ce" ni ba tsarar yaro bace, ni na haifi ubansa kinga kuwa nai masa rata, bana son ina yawon yi masa magana dan kar ya raina ni, ke kuwa dan ubanki kika kuma ce min kakus muhammadu ne zai yi mana shara.a Momy ta girgiza kai ta yi gaba Yau kam samir har cikin banban falon Sudais yana bin Sudais da kallon mamakin irin masifar da yake zazagawa tamkar ya ari baki ya kasa zama waje daya sai kai kawo yake Ci gaba ya yi da fadin" ita ta isa? Wacece ita? Mai take takama da shi? Ya tsayin tsaurin idonta ya kai? Ni da na yi yawon duniya ai ba gwada min kyau zatai ba domin ba irin wada na gani! Ni har zata buda baki ta furtan bata so na? Nine ma bata so? Ni? To sai me? Mutuwa zan yi ne? Nima bana sonta na daina son ta kuma dole sai ta zauna da ni, sannan walahi sai na kara wani auren ta zauna ta ga yanda mata suke rawar kafa a kaina! Samir ya dago ya kalle shi, bai iya cewa komai ba sai shiru da yayi aman a kasan zuciyarsa fadi yake akoy aiki aure kuma? Sudais ya katse shi da fadin" ka je da kanka ka dauketa ka kaita vila gra, kafin ka karasa ka tabatar an kara gyara mata wajenta, a zuba dukan abinda zai sakata nishadi, Da mamaki ya kuma kallon sudais, aa shi kam baya gane inda yake nufa a duniya, yanzu ya gama hargowar ya tsaneta kuma yana fadin a kara kawata mata wajen da ko yar president zata ji ya yi mata 100/100, gannin fuskarsa a hade ya sa ya mike daidai su Humaira sun shigo dan ta dauki hijabinta, ita kam murnar kauran nan take domin kuwa gidan nan a ce gidan mijinta ne ta faso fa, ta mugun faso sannan daman ya shaida mata ba abinda zata kai idan an tashi kaura ya zuba komai tun daga kan kayan daki kicin da sababin suturu Da murnarta ta dauko hijabinta ta fito direba ya dauke su sai Gra Da salama ya shigo gidan yana kwalawa, da kyar ta iya mikewa ta fito sai gannin Samir ta yi Da dukawa ta yi tana gaisar da shi ya amsa yana fadin ta mike ta mike Cike da girmamawa ya sanar mata umarnin ogansa kan ta fito a kaita gidansa Da tsoro ta amsa ta juya dan kwaso kayanta Dakatar da ita Samir ya yi ya ce" Hajia ya ce ki bar komai a nan Murya a raunane ta ce" aman bawan Allah gadona da kujeruna da labulayena fa? Samir ya yi murmushi ya ce " za.a kawo maki hajia yanzun dai mu tafi Dakin ta kala da kyau, da wayarta a ciki wace da zata taho ta baiwa aisha numberta duda basu nemeta ba aman tana son rikewa ko zasu neme ta? Sannan ina za.a kaita ne haka? Ko har zai fara gabatar mata da niyar tasa na kuntata mata? Idannuwanta ta lumshe bayan sun dauki hanya sabon hawaye ya tsiraro mata daga kurmin idonta a ranta ta furta " ALLAH KA CECE NI YA JIKAINA YA ALLAH *❣IDAN KA RAINA INDA KAKE❣* Na: *SAJIDA* *_LITATAFAN MARUBUCIYAR_* *_Duk Karyar kada_* *_Yar Mahaukaciya_* *_Neman na kaina_* *_Bani da zabi_* *_Daga tafiya daukar soja_* *_Idan ka raina inda make_* *🌈KAINUWA WRITERS✍🏼 ASSOCIATION*🤝🏻 ```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}``` https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation 31 *aa fa reader, comment dinku baya gamsar da ni, ba yawa a gaskiya na raina🤦‍♀, idan bai karbu bane nvl din nan sai na dakatar nima na yi uzuririkana😌, raina baya son rashin kula😁 so plz comment woh? Albishirin ku kawai yawan comment dinku tabatuwar typing wato nxt page in sha Allah😍😍😍😍* Tafe suke ta jinginar da kanta jikin madubin motar, abinka da rana fu irin sanyin motar sai da take jin dan zafin ranar a gefen fuskarta da ta kara jikin madubin A haka ta lumshe idannuwanta ta tafi duniyar runani wanda motar ke sheka gudu aman ita bata ganewa Lumlumlum ta ji ba ranar, sai kuma ta ji wata iska mai sanyi tana dan buso mata da kanshin shukoki A hankali ta bude idannuwanta a dan lumshe ai bata san lokacin da ta ware su dar ta bi wajen da suka shigo da kallo A tsorace ta waiga baya sai ganni ta yi sun shige wani irin get a cikin wani waje ne suke A matukar tsorace ta ja da baya ta kali gefen da Samir ke zaune daga gaba, tsoro ne ya kara kamata murya na rawa ta ce" Mmalan nan kuwa ina ne? Ina ne nan? Samir da ya lura da yannayin firgicin da ta shiga ya ce" sorry hajia, ai nan ne gidan Ido ta zaro ta ce" gidan wa?? Samir ya dan rage gudun ya dan juyo gannin sai juye juye take ya ce" nan ne *GIDAN KI* wato *GIDAN MIJINKI ELHAJ SUDAIS UBAN MASU GIDA* Wani yawu ne ta ji makwad ya fice mata ta makogwaro ba tare da ta shirya ba, har yanzu bata samu nutsuwa ba, what? Gidannan? Gidan da zata zauna na dan lokaci? Wannan gidan dama akou shi a kasar nan? Aman ya haka shiru sai jibga jiban dawissu da ake kiwo suna ta baza fifike sun fi karfin irgenta masha Allah, sai aku kuturu da ta hango can wani gefe suma masu dan yawa, Motar ta ji ya taka hakan ya sa ta bado hankalinta wajen sa Fitowa ya yi ya bude gefenta ya ce" bismillah Ta jima tana adu.a kafin ta yi tawakli da Allah ta fito jikinta a matukar mace sai kara kallon gidan take tamkar sabon shigowa birni Aman ya aka yi na ga abubuwan kiwo? Bana gannin mutane? Ina mai gadi? Samir da ya kunnawa Sudais komai tun zuwa daukota yana sauraron su ta karamar wayarsa ya ce" ba mai gadi, get din na anfani ne da command, Akoy ma.aikata sosai suna can bangaren su na maza daban na mata daban, sun bi umarnin oga ne na baya so suna yawace yawace har sai ya zauna, sannan wannan tsuntsayen ba su kadai ne yake kiwo ba, akoy kayan kiwo sosai a gidan an jejefa su ne bisa tsarin oga Shiru ta yi tana biyar bayansa har ya zo daidai wata kofar gilas wace ba.a gannin na ciki sai dai na ciki yana gannin na waje sosai, irin gilas din nan ne da bulet baya ratsa shi sannan duka baya yi masa sai wani ikon Allahn ke kashe shi Jikin mabudin Oga ya fada masa wajen da zai danna ya budu dan haka ya danna ya bude ya tura da dab karfinsa domin nauyin tsiya ne da shi Ita kam ta yi shiru biye kawai take da shi a baya Suna shiga ya yi salama Su Hafsat dake zaune suka amsa shi suna kallon wajen su Kanta a kasa hakan ya sa Hafsat bata gane ko wacece ba Humaira kuwa cike da gadara ta ce" wannan fa? Mai aiki ce ko me? Samir ya yi dan murmushi a kasan zuciyarsa yana ayana zaki fada ne wannan ta fi karfin ikon nan naki da kike yi mana dan kina matar mai gida tamkar kece mai kudin kina yi mana abubuwa tamkar wasu karnukan ki! Samir ya ce" aa, ba mai aiki bace, Daga haka bai kara ba gudun kar oga ya tsawatar masa domin ko daya baya bari a raina masa iyali ita kanta tana wulakanta su ne bayan idannuwansa domin itama bai bata damar ta wulakanta su ba, su kuwa sunai mata biyaya ne domin maganarta ta fi tasu tasiri a wajensa duba da darajar da Allah ya yi mata na zama matarsa abinda ya fi kisanci da shi a gidan duniya wato matarka ko mijinki Yatsina fuska Humaira ta yi, ita fa har ta gama cinyewa sai cin magani take tana kakauda kai ita ga matar Elhaj ta sha wani uban lesh baki ya kara fitar da hasken fatarta wly har kashe ido yake ta yi bau da ita aman kana yin kusa da ita karni zai kore ka ta ce" malan idan ba mai aiki bace ai sai ka jata ka koma da ita dan baya nan bare ka kwaso wata mai datin budurwarka ka kawowa mutane! Ta karashe ta a dan daga muryarta Jin abinda ta ce gaban Rauda ya kara faduwa da dan tsoronta ta dago dan gannin matar tasa ce? Ko matansa domin murya bibiyu take ji ta mata Hafsat ce ta dan kwalalo ido gannin Rauda, da murnarta ta mike ta nufo wajen Raudar ta ce" Lah, lale da yar uwata, auntyna Rauda ta sauke ajiyar zuciya domin har ga Allah irin yanda Hafsat ta taso har ta fara kokarin buya a bayan Samir dan ta yi tunanin ko dukanta zata yi? Rauda ba dai tsoro ba Dan murmushin da bai kai zuci ba ta yi tana dari dari ta dan rike hannun Hafar kamar yanda itama ta rike ta tanai mata murmushi Auta wacece ne? Ban ganeta ba Humaira ta fada itama ta mike tana karasowa tana bada hankalinta wajen su tare da fatan ba wata ta jiki bace sosai kar ta je ta fada bata yi masu tarban kirki ba Aunty, Aunty amarya ce fa, Hafsat ta bata amsa fara.a konce a kan fuskarta tana jan hannun Rauda dan ta karasata wajen makamakan kujerun falon wa.inda kala har hudu ne maka maka saiti hudu an mugun tsara su kalar tsanwa mai duhu da fari haka labulayen ma sun yi kala daya da kujerun sai wasu tafka tafkan tableau kwaya shida an jejefa su da wani tafkeken zanen zaki da akai a jikin bangon wanda sai ka rantse mai rai ne domin an yi shi ne da komai irin na ainahin zakin na gaske sai wata tv wace da ba dan tana haska hoton namomin dajin da suke kallo ba da sai ka rantse ba zai yiwu a yi tv mai girma irin nata ba tamkar a cinema ta cike bangon gaba daya sai wasu tafka tafkan Peau de fleur kwaya biyu farare kar sai dan kyalin tsanwan da suke an ajiye su gefe da gefen tvn wace du tsayinta sun kai daidai tsayinta ( uhum wasu kayan sai amale ) sai abin turaran wuta mai kalar dawisu an baza fikafikensa wanda ta nan hayakin turaran ke busowa a hankali an saka su har kwaya hudu a kowace kusurwa ta dakin Sai capet mai kamar shukar ciyayi an tsara shi tamkar zanen mutun an zagaye shi da fari farin ciyayi a tsakiyar kujerun nan bai cika tsakiyar ba sai ya kara haska tiles din falon fari kar mai dan Garza garza, sanyin ac din palon ne ya saka ta dan kara kankame hijabin dake jikinta sai wani sanyin kamshin da ma.aikata ke kula du mintuna sai sun dawo sun jona sun saka turaran wuta sun fesa na ruwa mai sanyin kanshi Humaira ta ce" eyah, ai ban ganeta ba Auta, wace auntu amarya? Ko na ce ta ina? Hafsat ta ce" kai Aunty, ta gidannan mana matar yaya Jin maganar Hafsat ta yi tamkar saukar aradu a tsakiyar kanta, kuturun uba, matar wa? Ba yace sai an yi adu.ar matarsa zata tare ba? Wai ma ina wa.inda suka rakota? Sannan wannan yar kauyen ce ya aura? Me ke damunsa? Bata ankara ba sai gani ta yi Hafsat na kokarin zaunar da Rauda saman kujerar falon Da mugun tarashi ta furta" ke hafsat kar ku karasa kar ku saki ku karasa A tare suka ja suka tsaya da dan alamun tsoro a tatare da su don kuwa ita kanta hafsat ta yi tunanin ko wani abin ne ta gani Da sauri ta daga kafarta ta karasa wajen su, hannunta ta kala da mugun kyankyami ta kama gefen hijabin Rauda ta jawota kiiiiiii har daidai kusa da Samir wanda yake tsaye da mamaki yana kallon lale Humaira ta samu fada a wajen oga aman bata san darajar Mata ba Cika ta ta yi wanda har Rauda ke dan haki na mugun saurin da ta yi ta biyo bayan Humaira da kuma bugawar da zuciyarta ta yi na tsoron me haka kuma? Humaira ta cika hijabin tana nuna kyankyamin hannunta , Taku daya biyu uku ta yi ta dan zagaya Rauda tana dan tafa hannayenta, Wata dariyar tabara ta saki irin na an goge din nan ta ce" ke? Ke ce kishiyata? Lale na yarda kadara da rubutun tun ran gini tun ran zane! Bakar kadara ta kawo ki auren mijina? Sannan abin mamakin kin tare ke kadai ba dangi hakan na nuna min an gama sannin juna tun a kofa? Da sauri Sudais ya rintse idannuwansa domin du abinda ke faruwa a kunnansa, mamaki, da al.ajabin dan adam ne ya kama shi , shi? Shi ne Humaira ke jifa da kalaman nan da zargi? Sun gama sannin junna? A tunaninsa irin yanda ta san ko shi waye ciki da bai ba zata iya yarda ta furta wannan kalmar kansa ba, murmushin takaici ya saki yana ayanawa ransa ya sani ba zai yi shaidar Mata ba, aman zai iya shaidar kansa, um ita Humaira ta sani ne da ace mata nake bi da bata layin macen da zata wanken takalmina bare har ta san sirinA nonsense kawai Katse masa tunaninsa ta yi inda take fadin" ki sani, ni Humaira sai na zame maki jaraba masifa balakin da zai saka ki hadiyi zuciya ki mutu a tarar da gawarki! Mijina nawa ne ni kadai , ke koda zan raba shi da wata sai yar masu fada a ji ba wai ke ba yar talakawa! Dan haka hanyar da ta kawo ki ta maida ke inda kika fi wayo Haba Aunty, menene haka kike yi wai? Tamkar marar ilimi? Hafsat ta furta domin Rauda ta bata tausayi irin yanda take hawaye kanta a kasa tamkar ta yiwa sarki karya ita kuwa Humaira sai kara hargowa take tamkar tanaiwa yarta fada Sam abinda ta yi bai baiwa hafsat mamaki ba domin ta santa da rashin kamun kai zata iya yin fiye da haka ma sai dai tausayin Rauda ya sa ta yi mata magana Kin ga, Hafsat ki fita a maganar nan, ba abinda ya shafeki da abinda nake yi a gidan mijina ehe, ni ai har na shiga fargabar kar a je ya auro min wata big girl ne ashe tsami girl ne, no bani da wajen zamanta a gidana Murmushi Samir ya yi jin abinda SUDAIS ya fada cewar ya gwadawa Rauda dakinta gayanan zuwa gidan, Ya tabata a yanda ya yi maganar a kausashe sai ya ci uban wannan mai karyar rashin kunyar Wajen rauda ya kallo ya ce " hajia mu je ga dakinki can inji Oga Da sauri Rauda ta bi bayansa domin daman jira take tamkar ta tashi sama dan sauri haka tsoron Humaira da haukanta ya darsu a ranta Da sauri ta shige bayan ya danna wasu number ya bude mata dakin tana shiga ta turo kofar da karfinta irin dai ta shigowar ce ana gannin na falon ba.a gannin na ciki Tsaye ta yi dan nesa ba tare da ta lura da irin aljanar duniyar dake dakin da aka kira malakinta ba ta tsurawa Humaira ido yanda take ta masifa har dira take tana kumfar bakin yau ko ita ko Rauda sai ta bara mata gidan mijinta Hannayenta biyu ta dora a saman kanta ta silale saman kafafuwanta, a fili ta furta" *wayo Allahna ni Rauda tawa ta same ni, Abanna kana ina Abanna ? Aba wannan bawan Allahn shi ne Aunth Aisha ke matukar so, shi ne na daga hannu na mara, shi ne ya tsane ni tun kafin mu hadu da juna, shi ne mai arzikin da ko a kafarsa aka kula masa ni zai cire ni ne ya yar, matarsa mahaukaciya ce tsoronta nake Aba, Abana bana son sa, bana sonsa Abana bana son fitinar dake tatare da shi, SHIN YAYA ZAN YI?* *❣IDAN KA RAINA INDA KAKE❣* Na: *SAJIDA* *_LITATAFAN MARUBUCIYAR_* *_Duk Karyar kada_* *_Yar Mahaukaciya_* *_Neman na kaina_* *_Bani da zabi_* *_Daga tafiya daukar soja_* *_Idan ka raina inda make_* *🌈KAINUWA WRITERS✍🏼 ASSOCIATION*🤝🏻 ```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}``` https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation 3⃣2⃣ *ALHAMDULILAH YA ALLAH,* Haikewa Aisha ta yi tana fadin" in ba jaraba ba irin na maza mai ya gani a jikin wannan? Idan farin ne gashi a gidansa, kyan na tara mai ya rude shi? Ta juyo wajen su Samir ta kananage ta hana Samir fita ta hana Hafsat magana sai masifa take wai taya ma za.a baiwa wannan yar talakawa mai datin wannan dakin? Ita ta tabata ya fi nata dan haka ba zata yarda ba ita ce baba ita zata zaba kafin ya zuba wanda yake so Kan samir a kasa yake yana sauraron yanda Sudais ke gudu da mota, a ransa kuwa yana fadin da ba.a san asalin balbale ba da ta ce daga turai ta fito Bata ji karan shigowarsa ba tana ta masifa sai ganinshi ta yi Dif ta yi da magangannun da take tana kalon sa sannan ta dan matsa da sauri kusan Hafsat Kofar Rauda ya kala ya ga daga ciki tana gannin na waje domin yana iya canza abin ya dawo na waje ke gannin na ciki, dan haka ya sakarwa Humaira murmushi ya kali samir ya salame shi Hannun Humaira ya rike tamkar suna maganar soyaya yana dan murmushi ya jata har zuwa dakinsa Suna shiga ya tabatar ya rufe ya hankadata wanda ya saka ta yi tagatagal ta fadi kusa da bed, kansa ya dafe yana tir da irin halayan Humaira, sai ta saki baki ta ringa fadin magangannu mararsa tsari sai daga baya ta yi zuru zuru, tabas zai ringa biye mata har ya ga wacece ainahin wada ta haukata zuciyarsa haka kafin ya mugun daukan mataki a kanta Taku ya yi zuwa da zauwa ya kai sau uku ya tsaya daidai inda take, murya a matukar kaisashe ya ce" ki iya takun ki Humaira, ki iya harshen ki, ki kiyaye ranar da idannuwana zasu rufe kan izgilancin ki, ki kiyaye shiga sabgar *SIRINA* Yana gama fadar haka ya juya ya fada bayi Shatata ta yi da baki ta bi bayansa da kallo, ya aka yi ya ji abubuwan da ta fada, me yake nufi da *SIRIN SA? WAYE SIRRIN SA?* tunda ya shigo ta tsayar da kukanta ta zuba masa ido wanda ita kanta bata san ta yi ba, tana gannin tun budewarsa da shigowarsa , du irin tijarar da matarsa ke yi sai ta ga ya sakar mata murmushi ya ja hannunta ya yi daki da ita harma da alamar ko fada ya yiwa Samir? Wani irin gum ta yi ta rasa tunanin mai zata yi, ita kanta ta san Sudais ba tsararta bane ya fi karfinta nesa ba kusa ba, sunanta da nasa basa kama da juna , matsalolin dake tsakanin tarayarsu ta girmameta, Aisha Aisha, Humaira A hankali ta juya dan ta samu ta nutsu sai dai kara waro ido ta yi, Wannan fa? Ko dai Samir bai gane inda aka ce ya kaita ba? Daki ne ciki daya, sai dai girmansa ya isa a yi ciki uku da shi, ba komai sai makeken bed da wani abu tamkar runfa a samansa, an yi masa shinfidar alfarma iri daya da jikin bangon dakin wato fari, labulaye ne a jikin runfar wa.inda take kyautata zaton Ana sakin su ne Sai gefe daya wajen gabas da tapi na sallah da dan table na silba mai kyalkyalo samansa kur.ani me da litatafai Kara kallon bed din take da dakin, mamaki take wannan tankamemen dakin na wane? Dakin kadai ya kai girman gidansu harda dakuna Kanta ta kai gefen bed din daga sama sai ta ga wasu manyan buton da rubutu a jikinsu A hankali ta matsa tana adu.a abinka da mai ilimi ta karanta, Hannunta ta mika ta danna wanda ke nufin bayi, ai kuwa sai ga kofar bayin ta bude wanda hakan ya sa har ta tsorata, ta yi saurin rufe shi ta kuma danna na kusa da shi sai ga armoire ya bude, sutura dai mai sunnan sutura shake a ciki, kwalalo idannuwanta ta yi ta girgiza kanta kawai ta rufe ba tare da ta matsa ko kusan kayan ba, Haka dai ta yi ta zuba kauyancinta tana kara bin dakin da kalo , ba wani katsamniya sai sanyin ni.ima dake tashi A dan hanzarce ta kuka bude bayin ta shiga, nan ta ga idan da mutun dole sai shi zai bude ya fito aman wani ba zai dana ya kara bude masa ba Rufewa ta yi tana bin bayin kansa da kallo, a fili ta furta" tamkar ba za.a mutu ba, tamkar wannan watarana ba zai dawo kasa ba, tamkar kasa ba zata linke shi ba A hankali ta cire hijabinta, ta tube ta shiga kasan shower wanda kana shiga kasan sa zai bada ruwa kana fita ya tsaya, da ba dan ta ji yan ajin su da Aisha na fadar wasu abubuwan ba da ta kurma ihun tsoro A hankali ta sabe jikinta da sabulun ruwa da sabon soso fari kar har gashin kanta, Tana gamawa ta dauro alwallah ta yi tsaye wajen kayan da ta cire , dauka ta yi kawai ta mayar da abinta ta fito a hankali ta zauna kan darduma ta dauki alkur.ani mai girma ta shiga karantawa da kudirin yana zuwa zata roke shi da ya sawake mata, ta bashi hakurin abinda ta yi masa (uhum.....) *Me ya gani a jikinta in ba jaraba ba irin ta maza !* maganar ta kuma dakar dodon kunnen Sudais wanda ya yi tsaye kasan shower tana ta zubun masa saman lalausan gashin kansa Idannuwansa ya bude tarrr ya tsurawa waje daya ido, A kasan zuciyarsa yayi murmushi, ya shiga bin miscle din jikinsa da kallo, dukan wata gaba ta jikinsa ruwa na sauka kanta yana binta da kallo, wani murmushin ya kuma saki a fili ya furta" she is yng Sudais ba wani abokai ne da shi ba bale ya ji zantutukan yau da kulun na rayuwa, A film kuwa du abinda zai kala ya dauke shi a matsayin karya domin yana kallon film din turai, wai zaka ga wani wajen sunna koda wannan harkar shi dai sai ya yi murmushi ya fice wajen, KHAIRATH marigayiya ta kasance mace mai jiki sosai, yar lukuta ce ta gaske wanda tana son kai shi wajen da ba.a dawowa ma aman sai abin ya yi mata wuya yannayin girman jikin Ita kuwa hajia Humaira abubuwan sun taru sun yi mata yawa, shegen son jiki ita sai dai ta sankame masa, ga warin man bleating din nan wanda ta dorawa kanta!, ga dan uban ciko ita ce acuci na gidan nono ita ce na baya , gashin kanta a kulun cikin saka kari take, idan ta tube yanda ka san tabarwa bata da tsari ko wani abinda zai fizgeka gareta , SUDAIS ya kasance yana shan ruwa ne dan korar da ishirwa kar ta kar shi bai san banbance dadin ruwa ba bai iya banbance ruwan tafki na rijiya da na pampo ba shi dai kawai gugarsa yake sakawa ya ibi ruwa ya sha, abinda ya sani daya ne, karamar randa tai masa kadan, Idannuwansa ya lumshe ya fita daga kasan pampon ya dauki fari kar din towel sabo fil ya nado iya kugunsa ya fito ya zauna gefen bed, Shiru yayi ya hasko Rauda a idannuwansa, shi dai bai taba ganninta da garamar shiga ba, ainahi ma idan ba zumbuleliyar doguwar riga wace watan takan dan matse mata daidai mama watan kuwa yanda ka san buhu a jikinta sai zumbula zumbulan hijabai wanda ba zai iya tantance ya take ba domin iya tsintsiyar hannunta kawai ya iya gani a zamansu tun lokacin da ya fara ganninta har zuwa yau ba, ba zai iya sifanta ta ba, Lumshe idannuwansa yayi, a fili ya furta" yarinya ce, abu na farko da zai hana na sota dan wani abin na jikinta kennan domin na fi karfin taraya da yarinya karama, ya kuma sakin murmushi a kasan ransa ya ayana ko harbawa ba zatai ba idan na taketa, wly ko motsi ba zatai ba zata je inda ba.a dawowa, Wani murmushi ya kuma saki ya ce" baby , na baby girl, no Humaira ba dan jikinta na aureta ba ba dan kyau ko wani fari dake daukan hankalinki ba ni kaina na rasa takamaimai abinda ya sa nake kaunarta, just na wayi gari ne cikin bakon yannayi, na farka ne na tsinci kaina a halin soyayarta, abinda na yi ta kaucewa ko nace na yi ta tunanin ba zai faru da ni bane ya faru da ni, ina tsananin son *MATA* Ko ya Raudat take? Mama ke zaune tana zancen zuci har ya fito fili Aisha dake mike saman tabarmar leda tana dadana yar karamar wayarta ta tabe baki , ita fa mama ta fara isarta, shi kennan ita daga an zauna sai tunane tunane da tambayar infa Rauda take? To siyar da ita za.ai ne ko me? Ba aure akai mata ba? An hada ta sabuwar rayuwar talauci ba dole ta labe ba Mama ta kai dubanta wajen Rauda, a ranta take aiyana" Allah sarki Rauda, da tana nan ba zata bari na shiga kicin ba, ba abinda take bari na yi, ta wuni tana aikace aikace hakan ma cikin rigingimun gidan nan, ya Allah ka sa ta samu farin ciki a gidan da aka kaita a matsayin gidan mijinta A hankali ta kuma kallon Aisha, yau tunda ta farka ta karya ta mike kafa saman tabarmar nan ko tsinke bata dauke a gidan ba, aiki kamar ya kashe mama sai dauke nan ajiye can take , yanzu kwatakwata basa wani dasawa da Aisha, ko dama dan tana gannin Rauda ne take like mata ita kuwa tana ture Rauda? Ita kam takan rasa kan Aisha, Bata gama tunaninta ba Sarah ta yi salama Aisha ta mike da saurinta ta tarota tana murnar ganinta Sarah ta yatsina fuska ba tare da ta gaishe da mama ba ta ce" ke yanzu baki ma shirya ba me kike ne haka? Aisha tamkar zata shige jikinta take fadin" ai kayana kawai zan saka ki shigo na saka mu tafi Sarah ta yatsina fuska ta ce" aa aa, na zauna a ina? Ke dai je sako kayan mu je Tana gama fada ta jiya ba tare da ta gaishe da kanwar mahaifiyarta ba ta nufi motar mamanta da ta dauko A gurguje Aisha ta fito ta ce" mun tafi sai mun dawo mom Mama da baki wangale ta bita da kallo, a ranta take ayana ina kuma zata je? Me suke aikatawa ne yaran nan? Rauda ta wuni karatun alkur.ani wanda tana gamawa ta bingire a nan baci yayi awon gaba da ita Hafsat ce ta shigo dakin bayan ta jima a falo har magarib ta shigo bata ga fitowarta ba Tausayinta ne ta ji ya kamata, gannin hijabin nan dai shine a jikinta, gaskiya ya dace ace ta canza domin kuwa da ganni ya jima a jikinta sannan Samir ya kawo mata akwatin tufafinta domin sudais ya bada umarnin a kawo mata ko dan ya kara gannin halayenta sai samir ya canza kano ta yi zahin ya zuba kayan a akwati A hankali ta karaso kusa da ita ta duka ta shiga tashinta ta hanyar dan jan hijabinta tana fadin" aunty amarya aunty amarya Firgigit Rauda ta farka a bacin da take mai dadi ta kali Hafsat, dan ja da baya ta yi tana kokarin tashi du a dan firgice take domin bata ji shigowarta ba ko dan bata samu isashen baci jiya ba sai ta yi shi tamkar ta mutu a yanzu har aka shigo bata ji ba Hafsat ta dan dago hannunta ta ce" Aunty lafiya kuwa? Rauda ta yi dan raurau da ido, ta sada kanta kasa tana kokarin saita bugun zuciyarta domin ta tsorata ainun ta yi tsoron ko matarsa ce? Ko shi din kansa aman da alama kanwar nan tasa tana da mutunci Dan girgiza kanta ta yi alamar aa, ba komai Hafsat ta sakar mata murmushi ta ce" ki tashi ki canza kayan nan Aunty sai ki fito ki ci abinci, baki ci na 12 ba har dare ya kawo Rauda ta sauke ajiyar zuciya murya na rawa ta ce" kakayana ban dauko ba Hafsat ta yi murmushi a kasan zuciyarta take ayana innocent Kayan ta miko mata ta fice ta bata waje Ba tare da ta sake wani wankan ba ta canza kayan jikinta ta saka daya cikin atampopin da Abanta ya dinka mata, Wa.inda ta cire ta koma bayi ta wanke ta sarkafe jikin karfen da ake shanya towel Fitowa ta yi daga bayin tana fan tsane hannunta tana gyara daurin zanin dake jikinta bata lura da mutun ba sai da ta dago da kanta ta ganshi tsaye ba fuskarnan tamkar zaki ya hadeta ba alamun wasa a tatare da shi Gabanta ne ta ji ya mugun buga mata wanda har ta saki.....m *❣IDAN KA RAINA INDA KAKE❣* Na: *SAJIDA* *_LITATAFAN MARUBUCIYAR_* *_Duk Karyar kada_* *_Yar Mahaukaciya_* *_Neman na kaina_* *_Bani da zabi_* *_Daga tafiya daukar soja_* *_Idan ka raina inda make_* *🌈KAINUWA WRITERS✍🏼 ASSOCIATION*🤝🏻 ```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}``` https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation 3⃣3⃣ Kabewa a dafata ta dafe a murjeta sosai ta yi kitib a hadata da madara peak da karankafi a saka a firij ya yi sanyi a sha da safe kafin lokacin zuwa turaka , kana iya sha ko ba sanyi zabinka ne🚪🚪🚪🚪🚪🥰🥰🥰🥰 Gabanta ne ta ji ya mugun faduwa, wanda har ta saki dayan hannun zanin da sauri ta raruma ta daura haka kuma jikinta ya dauki rawa domin ba hijab a jikinta danma Allah ya taimaketa dinkin Aba da ya kai gaba daya manyan dinkuna ne akai mata du idan ta saka zubul take yawo a ciki aman wuyanta da yake a bude sai tana jin tamkar ana gannin sauran sashin jikinta Kalo irin na kurulah ne ya kafeta da shi wanda shi kansa bai san ya shagalta da kalonta haka ba, so yake sai ya karanto abinda ke saka shi afkawa a soyayarta har haka , yanzu ma wannan kayan na jikinta tamkar ta aro sun mugun yi mata yawa baka iya tantance ainahin tsarin jikinta Ya kai sau uku tana dan dago idannuwanta tana satar kallon sa sai ta ga ya tsura mata ido tamkar yana hararanta Kanta ta sada a karo na ba hudu tana dan murza yatsunta Ajiyar zuciya ya sauke, a kasan zuciyarsa yake ayana" inama wannan sabanin bai shiga tsakanin mu ba, inama kin fahimci irin macewar da na yi a kanki kin fito kin furtan kalmar so kin amshi tarairayana, Rauda sonki kawai nake Takawa yayi har zuwa daidai inda take ya ja ya tsaya, ya hade girrar sama da ta kasa ya ce" fatan kin shigo gidan aure dan bautar aurenki ba dan hutu ba Bata iya cewa komai ba sai zuciyarta dake ingizata kan ta nemi sakinta tun kafin tafiya ta yi tafiya, Sudais ya ci gaba" ina so idan ina magana a ringa bani amsa Kanta ta dan dago sai ta ga kusancin nasu yayi yawa dan haka ta dan ja da baya sannan bata bashi amsar da yake jira ba Kankance idannuwansa ya yi ya ce" ko baki ji abinda na fada ba? Kanta ta daga irin ta amsa shi, itafa a kasan zuciyarta bata ma yarda cewar shi din ne mijinta ba, me hakan ke nufi? Abanna ko bai san wanda ya aura min ba Hum ya ce , ya taka ya karasa wajen armoire Bouton ya mika hanu ya dana gaba daya suka bude, tsai ya yi yana bi da kallo kamar yanda ya umarta ne kuwa? Wato tufafin da ya umarta a zuba masu tun daga abaya , lesh, shada, atampa, kananun kaya, su bra komai an zuba yanda yake so masha Allah, ya juyo ya kuma kallonta, murya a dake ya ce" idan dai kina cikin gidana ya zame maki tilas ki yi anfani da suturar da na tanadar maki da kuma abincin gidana, Ya zama tilas ya kasance kina fita falo koda baci ne ki yi a can domin bana son ana yawan kunshe kunshe a daki Da safe karfe bakwai du abinda kike ya kasance idan ranar da .... ya yi shiru yana kallonta domin sai ya ji nauyi ce mata ranar da take da shi, haka gabzaza a gabanta a tsaye har zai ce mata wani ranar da take da shi? Ta ce me kennan? Wannan karamar yarinyar ai hankalinta ba zai dauka ba danma may be a islamiya an karantar da ita ko a makaranta an dan fada mata wani abin...., yatsina fuska ya kuma yi gannin ta dan dago jin yayi shiru, ya kawar da fuskarsa ya ci gaba" idan har ya kasance ranar aikinki ne, shayi da towel da ruwa mai dumi kin tanade su kafin lokacin, zaki kawo min dakin motsa jikina na gama ki tayani shiryawa Da sauri ta kuma dago kanta ta sauke idannuwanta a kansa, mamakinsa ya cikata , na taya shi shiryawa? Me yake tunani ne da ni? Kar ki yi wani tunani ko ki fasara ni a wata fuskar, ba dan wani abin ya sa na sako ki a layin matana ba sai dan na san hakokin Aure!, ba dan ina son ki ba, lalalalallalalalla ,....... Sudais ya fada yana dago mata dan yatsansa na kusan babar yatsarsa alamun maganarsa hakan take, sannan haushin kansa du ya tornike shi, ya haka sai kace wani redio ya sakata gaba sai zuba yake tamkar wani sauna ya kasa yin shiru du dan ta yi magana ya ji muryarta aman dan isa sai dai ta dago ta wani kale shi , kai da abinda take ayanawa a cikin zuciyarta sam ban yarda da wannan shirun da wannan kallon rainin da take yi min ba, waima ni ina tawa isar? Ni Sudais da idan magana ne sai ina iya yin minti ashirin kafin na tofa maka a yau na zazaga mata Magangannun da ina iya yinsu a tsayin wuni ba tare da na kara wani abin ba yarinyar nan ta kasa furtan wani abin, ta kasa yi min magana da muryarta na ji muryarta, rabona da muryarta tun dazu da Samir ya kawota ta waya idan ta dan yi masa magana, ya salam ni kuwa bana so na cika yi mata magangannun da zata raina ni """ Sudais ke ta fafatawa da zuciyarsa Gannin ba zata tanka ba ya saka shi juyawa da niyar tafiya A daidai wannan lokacin kuwa Rauda ta gama yanke shawararta, to ai ta fadi gidan sauki, shi baya sonta itama bata son sa, sai ya sawake mata kawai ta kara gaba , rigingimun dake tare da shi sun fi karfinta Murya kasa kasa cikin zazakar muryarta da yannayin sanyi kamar yanda ta saba ta ce" sire Ja yayi ya tsaya, ya saki ajiyar zuciyar da bai shirya ba, haka kuma ya tsinci iska na taba lebensa kennan harda murmushi ya saki , ya dan yi jim ya saita kansa kafin ya juyo ya dawo kusa da ita A hankali ta matsa kusa da bed din dakin ta ja ta tsaya , kanta ta sada kasa ta rike gefen rigarta dan samun kwarin guiwa, Tamkar ba zatai magana ba ta ce" ka yafe min, ka yafe min..., na aikata maka kuskuren da na yi nadama daga baya, Auntyna ta kasance tana kaunarka tun ba yau ba , sai haka ta faru... Sire tunda ya kasance ba wani abin da zai sa mu jure tashin hankalin da ya hada mu, *BA SOYAYA* , aure yinsa halal ne haka ma barinsa Abannnnn Shut up! Shu...u...shuppppppppppp! Sudais ya daka mata tsawar da hanjin cikinta ya hautsine Taku ya yi ya tsaya a daidai inda take, Bata san isowarsa ba haka kuma bata ankara ba sai ji ta yi ya saka hannunsa daidai wuyanta ya turata da karfin da ya bata mamaki wai haka ma bai yi mata da dukan karfinsa ba Kafarsa ya saka kadan ta bayan kafarta ya kaita saman bed din ya kasance ta fada rairan kafafuwanta a kasa daga daidai tsatsonta har kanta saman bed Kafarsa ya dago da takalmin kafarsa da komai ya dora gefen cinyarta wato ya raba kafafuwansa ya saka nata tsakiya, Nan da nan idannuwansa sun canza kala, kamanunsa sun zame mata abin tsoro, Kansa ya dafe wanda ya shiga sara masa , ta rigarsa kuwa kana iya gannin yanda kirjinsa ke dokawa zuciyarsa ta kara bugu Dan kwalin kanta ya fadi tun wajen faduwar da ta yi ta rinrintse ido gaba daya jiran duka take jikinta sai mugun rawa yake, Muryarsa a matukar dake tamkar ta zaki ya nunota da yatsa daya ya ce" *KE CE TA FARKO A WANNAN SASHIN, KUMA IN SHA ALLAHU KE CE TA KARSHE! KAMAR YANDA NA SAN ZUFATA TAWA CE HAKA NA SAN KE KIN SHIGO RAYUWANA, NA CIRE KADARAR UBANGIJI IKON ALLAH YAWA NE DA SHI KO MUTUWA, AMAN KI SANI BANA AUREN MACE NA SAKETA KE KODA KADARA TA SHIGO NA SAKE KI ZAKI ZAUNA NE HAKA DOMIN SIRINA MAWA NE!* hannayensa ya dora ya sakata a tsakiya, a hankali ta bi hannayen da kallo wanda tsoro ya sa ta shiga rawar jiki, girman hannayensa sun tsoratar da ita, sannan magangannunsa sun sakata a duhu, wai ma me magangannunsa ke nufi? Ita da bata kai karshen maganarta ba ya hazurka haka ina da ta kai karshen maganarta, me ke damun Uban gidanta ne, ya Allah wannan mutumin haka yake gabjeje da shi, sannan kanshin turaransa da ya doro hannunsa sai take ji ya cika mata hanci tamkar ita ta fesa Tar ta sauke kwayar idannuwanta cikin nasa dan gannin mai zai yi mata da ya kawo hannayensa haka? Gannin sosai fuskarsa ta kusanto tata ya saka ta rintse ido bugun zuciyarta ya ninku, sai da ya kawo fuskarsa daf da tata, ya zuki numfashinta ya sakar mata nasa itama ta zuka domin ba yanda zata yi ta kawar da fuskarta aman ta rufe idannuwanta ruf dan tsoro, A hankali ya kai bakinsa daidai kunanta ya sirinta muryarsa ya ce" *HUKUNCIN IRIN WANNAN FURUCIN MAI TSAURI NE MATA,* irin yanda ya yi maganar, irin yanda ya sakar mata numfashi a kunenta, yanda ya yi salon maganar nasa sai da ta ji wani irin yamyamyam gaba daya jikinta ya dauka, kan ta ankara ya fice ya barta nan konce tamkar wace ta yi dambe sai shesheka take tana sauke ajiyar zuciya ta rasa me zata yi ta ina zata fara 🤔🤔🤔 *❣IDAN KA RAINA INDA KAKE❣* Na: *SAJIDA* *_LITATAFAN MARUBUCIYAR_* *_Duk Karyar kada_* *_Yar Mahaukaciya_* *_Neman na kaina_* *_Bani da zabi_* *_Daga tafiya daukar soja_* *_Idan ka raina inda make_* *🌈KAINUWA WRITERS✍🏼 ASSOCIATION*🤝🏻 ```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}``` https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation 3⃣4⃣ A hankali ta mike daga koncen tana bin jikinta da kallo, kanshin turaransa ba wani taba jikinta ya yi iya wuyanta ne kawai ya taba aman jinsa take sosai a jikinta sannan tana jin dadin kanshin a ranta A hankali ta mike ta gyara zanin bed din ta dauko alkur.aninta ta koma saman salaya ta gabatar da salah ta zauna tana karatu har dare ya raba sannan ta konta a nan din dai ta yi baci Duk rintsi sai na kori yarinyar nan daga gidan nan mama, dalilinta yake min ihu a ka, mama kashedi ya yi min me hakan ke nufi? Shin sonta yake ko me? Haba Humaira, wai ke dai haka kulun damuwarki kennan kishiya kishiya kishiya? Ke ba zaki yi kokari mijin naki ya kasance kin zama sarauniyar zuciyarsa ba? Maman Humaira ta fada Humaira ta ce" mama, na rabaki da mutun mai kushe mutun, Elhaj fa ya kasance shi a komai sai ya nunan bai dace ba, ki duba fa ki ganni wai na tsayar da shafa mai, idan na tsayar fatana ba sai ta yi tamkar na kone ba wly sai ta dawo abin kyankyami ni kaina na sani aman wai shi Elhaj ya dage kai da fata sai na tsayar da shafa mai, kin ga yanzu yarinyar da ya auro din? Talaka tilis, sannan wly idan aka jeramu farina ya zarce nata nesa ba kusa ba sai ma ace yar aikina ce Mama ta ce cikin gagawar magana irin ranta ya baci" fari dai fari dai fari dai! Ke yaushe zaki yi hankali ki gane inda na nefa? Humaira da alama sai kin saka na fito fili na yi maki kwadokwado na marar kunya ko? To bara ki ji: Ku dai matan zamani yan mata da matan aure da yawanku burinku kyau, ki yi fari far ki yi dinki ki saka ki ringa kwarkwasa shikennan kyau ya kare kuma a tunaninki takamarki kyanki ya isa ya kaiki du inda kike so, ya isa ya ja maki soyayar miji ko waye, ya isa ya ja maki kulawar miji da sauransu, Ke kin san yau da gobe kuwa? Kin san kwana tare tashi tare kuwa? Uhum ke kin ga kanenki na yaba kaynki kulun? Ko a cikin gidanku kin ga ana raga maki dan kyanki? Ke ko a ma.aikata ya kasance an saba an san juna kulun kin ga ana daga maki kafa dan kyanki? Kina zaune ke mai kyau, mai aji, kina takama wata yar shila mumuna zatai maki shigar wuri ta raba ki da abinda kike takamar Ke idan baki kasance mai biyaya, hakuri, kawar da kai , tsafta, iya girki, iya zaman duniya da dukan wanda Allah ya hada ki da shi ta sanadiyar mijin nan naki...uwa uba sannin asalin waye shi mijin naki iya tafiyar da shi kofa a shinfidarku ne tofa a kulun kina cikin damuwa! Humaira mazan zamaninku da namu ba daya bane, ko a zamanin mu idan mace ta kasance baka gamsu da ita ba kana kara aure bale zamanin ku da matan ke harin mazan tun karfin su suna warto su suna nuna masu abinda suka kasa samu a wajen matar su ko ke ce mace ba dole ki kali wannan dadin ba? Ke Humaira idan fa shi mijin naki baya ra.ayin farar macen, bata bashi sha.awa kwatakwata baya jinta a cikin zuciyarsa sai ya kasance ke a hasken da Allah ya yi maki baki gode ba sai da kika kara kuma karawarma ta hauka Humaira har karni fa kike? Shi sakarai ne? Kina sairaron redio kina kallon tv kuwa? Kin ga yanda mijinki yake da daraja ya yi sunna a duniya kuwa? A zee aflan na ga talar shagonsa na chocolate, Humaira mijinki baban mutun ne wanda ya nema Allah ya yarje masa ya samu, mata ba kalar wace baya gani, ke har ya fito ya sanar maki ga abinda yake so aman ke sai ki yi masa kunnan uwar shegu? Ke ba zaki bi umarninsa ba sai kin jangwalowa kanki fitina ki dawo kina haikar baki tamkar wata mahaukaciya? Kina fa kallo irin yanda ake zaman auren a gidaje casa.in cikin dari, mijin ya auro macen ya sakata a gidan du dare ya dareta ya daneta ya biya bukatunsa da safe ya mike ya barta ba ci ba sha ga tarin yaya yau ba makarantar boko ba ta islamiya da kyar ta harhada ta samu jari ta dorawa yayan tallah idan sun saido sun kawo ta sayi kwaki ta kwada masu ya dawo ya cinye ya sha ruwa ya mike ya shirga baci dankareren kato idan ta raya masa ko abi kadan ya shiga tsakaninsu ya jibgeta a gaban yayanta ita kuwa ta yi ta kurma masa zagi ko ta yi ta hada shi da Allah ya isa yana kara lalacewa haka haka y'ay'an ma su taso sai idan Allah yataimake su wasu su dan kama sana.a wasun kuwa sai adu.a kawai haka suke fama kai da fata dan su samu idan dai ya fita ya dawo ya tarar da su sannan kar ya kauracewa shinfidar su, aman ke Allah ya yi maki gata ya wanke ya baki maimakun ki zagine ki dage ya kasance ke din wata ce a fadar zuciyarsa aa kina nan kina cafka bleating fata ta saka maki tamkar tsohuwa saman ido ya yakune maki gurbin ido yayi maki jajajir ya kode tamkar tsohuwar da ta kai shekara tamanin marar gata, ke daman abu ba abu ba kina fama da cikon nono da na mazaunai hannaye sun yi maki tauri tsabar masifar shafa mai ido du sun mutun maki jijiyoyin jiki sun firfito maki tamkar wata fatalwa gashin kai du atach ya cinye shi ya ja baya ya zama dan tsugul da shi a haka kike so ya zo yana sinsinarki? Ke hakuri ma ne da shi, yana da hakuri sosai. Humaira ke fa ba yarinya bace, shekara talatin da daya a duniya ya dace ace yanzu kin san abinda kike yi , kin zo da farkon auren ku kin garkama alura har ta shekara kina zuwa anai maki wai dan ko baya son haihuwa yanzu tun daga lokacin gashi sai nemanta muke kamar mu mutu babu maimakun ki yi fama da abinda ke gabanki aa ke kina tambayana yanda zaki yi ki kori matar da ya auro? Ki yi ta kanki ki haifa masa magaji mana sai ki taka da karfinki Humaira, ni dai fada maki nake a kulun idan kika kashe aurenki ba ke kafai ba mu kanmu kin yi mana bakin cikin rayuwar gata! Du wannan jawabin da mahaifiyar Humaira ke yi mata gajiya ta yi da sauraronta ta ajiye wayar ta sakata a handsfree ta dora wayar saman abin bed dinta kawai ta afka tunanin inda zata bi ta adabi rayuwar Rauda, bata da burin da ya zarce ta fice mata a gida ko ta sakata a uku Bayan sati guda A cikin wannan satin da aka yi ba wani canji da Rauda ta yi, ya kasance ma tana lure da wanda ya tunkaro dakinta sai ta konta ta shiga baci ko ta tayar da sallah ko kuwa ta yi bayi, harta Hafsat ta kasa sake mata ita kawai gani take ai sam sun fi karfinta ba zatai wata mu.amala da dayansu ba, du ta bi ta takura kanta ko abinci ya kasance ba wani sosai take ci ba domin hafsat ke kawo mata dakinta ta ajiye Abin duniya ya ishi sudais, a da yafi ganninta fiye da yanzu da take kusa da shi, yana cikin matsi da bukatar abincin ruhinsa, Yau karshen kwannan Humaira a dakinsa wanda ta caza shi ta kasa biya masa bukatunsa sai yake jinsa tamkar yayi tsere an fesa masa ruwa a iya fuskarsa kawai, sai jan ido yake yana muzurai gashi yau alhamis ne ranar kasuwa Tunda ya fito daga masalaci ya zo saka kayan training dinsa Iya kayan ya saka kamar yanda ya saba sai dai ina a yau fa sai ya yi dabarun maza Komawa ya yi ya saka wasu kananuwan kayan daga ciki ya dauko kayan training din ya saka iya wandon kawai mai ruwan Ash kala mai rubutun Adidas a jikinsa da bakaken harufa ya dauki rigar ya rataya a jikinsa ba tare da ya saka karama ko daya ba daga shi sai wandon dake jikinsa ya fito ya nufi wajen training Wayar da bata san da ita a dakin ba ta hau ruri dan haka ta zabura tana neman inda take, fitowarta kennan a wanka ta saka dogon wando jins ta saka riga fara kar mai kananuwan hannu domin ta san indai za.a shigo zata sani ne ta ajiye hijab a kusa da ita kiran ya shigo Rauda akoy son saka kananuwan kaya rashi ya sa take anfani da na gonjonta idan ta samu ta daya a dakinsu sai ta saka abinta ta sha iska ta yi karatunta ta sha bacinta da abinda, a yanzu da ya lamunce mata sakawar sai take taba kananun kayan har zumudi take ta saka ta yi ta murmushi domin tana son su halin yau da gobe ne sai a slow Tana daga wayar ta ji miryar sa haka kawai idan ta ji gabanta ke faduwa ya ce" idan baki cika umarnin da na baki ba a yau kina cikin fushin Allah Yana gama fada ya kashe yana ta kumbura ya ajiye rigarsa ya hau mashine ya danna ya shiga training Ta jima tana tunzura baki, bata son haka, sam bata son kusancinta da kowa Har ta bar gidan Kicin hudu ce a baban falon gidan kuma su biyun kowace da ky din nata dan haka ta dauki ky din ta dauko wani zumbulelen hijab baki sidik kakaura ta saka ya zo mata har daidai kafarta gashin kanta ya dan dago da hijab din yayi mata tamkar acuci maza Silifas ta saka ta fito ta yi saurin shigewa kicin din Baki ta hangame, ko.ina glas ne kana kallon kanka , zuwa ta yo ta taba sai ta ji ba glass bane bangon kicin din ne mai baka damar gannin kanka tamkar madubi Sai tsarin kicin din shi kansa ya kusan zautar da ita, Ajiyar zuciya ta sauke a fili ta furta" haka, aunty zata more 🙄 Kayan shayi ta harhada ta kuna gaz ta dora Ta dauko flask na inox ta kara daurayewa ta dauko papier ta goge sosai ta ajiye ruwan shayin tatare suka gama da ruwan gumin ta jujuye ta dora saman tire na inox sabo fil mai shegen kyau ta dora da kofofi tamkar shan mutun da yawa, tana yi tana ayanna dole na guji fushin ubangiji kafin mu fahimci juna ka sake ni! Kamar barauniya take sando kar matar gidan ta ganta ta wajen training din wanda daga sama aka rubuta shi din ma kofar dai iri daya ne Dana open ta yi ta tura Da hannunta na hagu ta shiga Tana shiga ta dan dakata tana raraba idon inda zata ganshi Saman wani tapi ta ganshi yana ta abdomino yana dagawa yana komawa muscle dinsa sun firfito, hannayensa tamkar na dan dambe yana yi A fili ta furta" tap! Tana zaro ido wanda bata san ta fito ba sai da ya dakata ya juyo da sauri gefen da take tsaye Tun daga yan yatsutsanta dake fili ya bita da kallo har fuskarta, ta sada kanta ita bata karaso ba ita bata juya ba ita bata ajiye kayan ba A ransa ya ayanna aa, yarinyar nan waima me take boyewa da take fama da hijabi tamkar wata mai takaba, daga ni sai ke a waje ki wani zumbulan hijabi to ko tubewa kikai kin isa ki girgizani ne? A dan harzuke yayi tima ya mike tsaye ya karaso inda take Ba tare da ya yi magana ba ya mika hannu ya karbi tiren ya ajiye nan gefe A hankali ya saka hannayensa biyu ya kama hijabin nata tun daga kasa ya shiga kokarin cire mata Idannuwanta ta kwalalo cike da tsoro ta yi saurin dafe hijabin ta shiga jujuya ido tamkar zata sume tana kokarin yi masa magiya tana jujuya kanta irin kar ya cire Nuna mata ya yi bai san yarenta ba, gannin tana ta kicikicin ya matso sosai daf da ita ya dage hijabin har wajen wuyanta ya furta" *ke, ki daina tunanin shirme mana, duniya sai ta nuna nake shanta!* Yana maganar ne yana idasa cire mata hijabin wanda dan karfin da ya saka ya sa ya biyo da ribom din da ta daure gashinta da shi, ta yo luuu zata fado masa ya ta yi saurin rike kanta ta ja da baya ta juya masa baya jikinta na rawa ta saki kuka mai karamin sauti ta tsugune jikinta na wani irin rawa OGA ELHAJ SUDAIS dai bai gane komai cikin mutuwa ya yi ko sumewa ya yo a tsaye a wajen ba, Wani irin zaro ido yayi ya sauke daradaran idannuwansa a kan halitar Rauda, Rauda ta kasance irin matan na masu diri, tamkar yar gwari haka duwaiwanta suke manya da su , tsatsonta kuwa dan firit sannan mamarta su ba manyan nan ba su ba kannanuwa ba a tsakatsaki suke , Gaba daya halitar jikinta sun yi daidai da tsayinta sun yi mata das sai idan tana tafiya ne jikinta rawa rawa yake tamkar iska na kada saka Yana nan tsaye tamkar bashi da jini ta rarumi hijabinta ta saka ta juya da gudu ta fice a wajen training din wanda fitarta kawai ya gani ya zabura ya....... 🤣🤣🤣🤣🤣🤣 *❣IDAN KA RAINA INDA KAKE❣* Na: *SAJIDA* *_LITATAFAN MARUBUCIYAR_* *_Duk Karyar kada_* *_Yar Mahaukaciya_* *_Neman na kaina_* *_Bani da zabi_* *_Daga tafiya daukar soja_* *_Idan ka raina inda make_* *🌈KAINUWA WRITERS✍🏼 ASSOCIATION*🤝🏻 ```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}``` https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation 3⃣5⃣ *Na fans na lv❤❤, ku yi min hakuri kunai min uzuri, abubuwan ne da yawa aman a koda yaushe burina na samu isahen lokacin da za.ina typing kulun, ku yi hakuri da wannan a yanzu in sha Allah za.a kara . Fatan za.ai min uzuri* *IDAN KA RAINA INDA KA KE GRUP, KUN SAN ME? JI NAKE DA KU, KUNYARKU NAKE SOSAI, KU YI HAKURI DA RASHIN JINA KULUN, ZAN GYARA DA YARDAR ALLAH, MUNA MUGUN TARE ... COMMENT DIN KU NA SAKA NI NISHADI* SADAUKARWAR WANNAN PAGE ga *SALMA, SHALELE, MRS SHUBADO, AISHA* Yana nan tsaye tamkar bashi da jini ta rarumi hijab dinta ta juya da gudu tana sakawa tana kuka ta fice a wajen trainin din wanda fitarta kawai ya gani ya zabura jin zai dima a kas ya raruri keken gudu😁 na sports ya damki karfen da hannunsa daya inda gaba daya jikinsa ya dauki rawa Sudais dai bai san adadin lokacin da ya dauka wajen training dinsa ba sai gannin Humaira ya yi ta shigo ta sha doguwar atampa mai kalar ja ja ta sha mak.up dinta sai kwarkwasarta take Karasowa wajensa ta yi tana fadin" husband, me kake haka a tsaye har lokacin office ya yi direba (tana nufin Samir domin biyayarsa da dadin sha.anninsa ya saka Sudais ya dauke shi suke yawo tare ba dan haka ne aikinsa ba sai dan aminci da yarda domin Samir ya karanci bincike ne shi ba lauya ba aman idan ya sako abu a gaba da yaradar Allah sai ya san me ya kumsa) ta ci gaba ya zo daukanka har yana falo a zaune, ni ina mamaki du yanda kake yiwa mutane iyaka da gidanka shi wannan har damar shigo mana falo yake ka kasa tsawatar masa Idannuwansa ya lumshe ya bude ya sauke su kan fuskarta, kallonta ya yi tun daga sama har kasa, gaba dayanta firit da ita wai kuma a nan ta cicika abubuwan da ta cicika A hankali ya cika karfen ya juya cikin takunsa na kakarfen namiji aman jiki du a sake ya dauko tawul din ya dora shi a kafadarsa kawai ya zo ya ratsa ta gefenta ya fice, Domin ta bashi haushi sam ita ba zata gyara halayenta ba? Ya zata shigo masa waje ba salama, ta zo bata gaishe shi ba bata ji ya ya tashi ba , ba wani magana cikin sanyi aa sai kace tana magana da kanninta ta zo ta yi masa tsaye a ka tana zazaga masa magangannu mararsa tsari kuma ita a nan fada take da gaskiyarta, to ke mace ke ya dace idan kin san da wani a gidanki da ba muharaminki ba ki lulube jikinki , ta fito ta gabanshi haka bata ji kunya ba sai shi ne zata zo ba tare da ta lura da yannayinsa ba ta rufe shi da surutu , shi kam ba za yana zama kulun yana fama da fada mata magangannu ba, shi ba sakaran namiji bane ta ci gaba da yi Bayansa ta biyo tana dan daga kafa, sarai ta san yau ba aikinta bane aman burinta ta je ta tsare shi kar banzar nan ta kusanto inda yake domin sarai ta san tunda aka kawo Rauda gidan bai taba hada shinfida da ita ba dan kuwa kulun tana biye da su Har dakinsa suka shiga, ta zauna saman kujera gannin yana shirin shiga wanka Da ido kawai take binsa ya dauki tawul ya cire baban wandonsa daga shi sai.......da ya sasaka ya tatatare.....abin nan ya nufi bayi dan yin wanka Sudais ya kai minti arba.in yana fama da ruwan sanyi , ya zuba ya kuma zubawa aman shiru ba alamar za.a sada masa, ba alamar za.a bar shi ya samu nutsuwa Cike da tsaki ya nado baban tawul dinsa ya karewa kansa kallo ya fito yana kara tamke fuskarsa Gannin halin da yake ciki a kasan zuciyarta ta ayana jarababe, shi dai kulun a cikin jaraba yake Aman da yake abin nata na neman fitina ne sai ta mike ta nufe shi, ba tare da ya ankara ba ya jita a jikinsa sannan ta nemi wajen da ya fi tsayar masa da tunani a wannan lokaci ta aniya hargiza masa tunani Sosai ya so hawa cajinta domin ya jima yana cikin bege, kwata kwata ya manta cewa ma ba ranarta bane yau, a inda yake tsaye ya lumshe idannuwansa yana sauraron lamarin da matarsa ta kai shi Kira ke shiga yana fita a wayar Samir ana tambayarsa oga, domin babar harka ce ta taso kuma gashi har karfe tara da kwata ba oga kuma ana ta kiran numbersa tana ringin aman baya dagawa dan haka aka shiga kiran number Samir domin suna kyautata zaton ko baya tare da shi ya san inda yake Dan murmushi samir ya saki ya ce " Hafsat, ko dai Oga ya fita? Hafsat ta waigo gefen Da samir ke zaune , ta kuma kallon kofar dakin Sudais, a ranta ta ayana aa bai fita ba, ban ga fitarsa ba fan haka ta mike ta ce da Samir tana zuwa ta nufi dakin Rauda dan ta zo ta dubo masa domin ta san yau zuwan RAUDAR ne Da kyar da sidin goshi Rauda ta mike a koncen da take Hafsat ta fada mata bukatarta inda Rauda ta zazaro ido tamkar ta ga dodo ta ce" ni ni kuma? Ni zan shiga dakinsa? Na yi masa me? Aa, dan Allah ki yi hakuri kar a je na jawa kaina matsala bayan wace nake ciki, Matsala Rauda? Mijinki ne fa? Kin kuwa san irin girman darajar da Allah ya bashi wace ya umarce ki.ke matarsa da ki yi masa biyaya? Rauda cikin tsoro da barar da baki ta ce" ke kin san me kike fada kuwa? Ta sha ikirarin sai ta kashe du wanda ya rabar mata abin kaunarta, sai ta ga bayansa, ta sha harowa mama cewar wly ta ba wasa take ba du wace ta yi gigin rabar shi sai ta halakata, ni ban taba sonsa ba, bai taba birgeni ba, ni ba tsarana bane ya fi karfina, ban taba sakawa zuciyata cewar ko na second daya zamu kasance mata da miji ba, nata ne , nima nawa a wani wajen ki yiwa girman Allah ki daina irin wannan maganar na tabata da ta sani da tuni na ganta na tabata haduwar mu ba zatai kyau ba, ina nan ne ina jiran Abana ya neme ni ya raba wannan hadin domin shi kansa bukatarsa kennan Hafsat mamaki da firgici ne ya darsun mata a zuciyarta, me hakan ke nufi? Matar da yaya ke matukar so da ita bama ta sonsa ko me? Sannan tsananin tsoron Humaira ne ya sakata irin wannan rikicewar? Sai kuma da ta furta daman shima baya so! Maganar ta yita a cakule ba tare da ta banbance wa ba? Abanta ko yaya Sudais? A hankali Hafsat ta karasa kusa da Rauda, ta kamo hannayenta ta jawota bakin bed suka zauna, kan rauda a kas tana ta shesheka da ganninta cike take da damuwa, sannan Hafsat ta girmi Rauda domin tsarar su Aisha ce, sai kuma yannayin tsoro da ta karanta a tatare da Raudat Ajiyar zuciya ta yi tana kalon yannayin Rauda, a kasan zuciyarya ta ayanna tabas girman rauda shekara 22 ya rigayi wayonta, koma wacece ke firgita Rauda harda wautarta, sannan da kuma ta karanci du irin tarin dukiyar nan ta gidannan da irin dukiyar da Sudais ya zuba masu sam baya dadata da kasa, da wata ce da ko dan wannan daula ta zauna, sai babar rigimar ta lura kwatakwata a yanzu Rauda bata son yayanta kuma bata san shi irin son da yake yi mata ba, da ta san irin yanda yake kokarin dane soyayarta karta fito fili ya zama tamkar zautace da ta ingiza zuciyarsa ya haukace mata ta ja linzaminsa, Abu daya zata iya yi dan ceton rayuwar Yayanta domin ta fahimci soyayar wannan baiwar Allahn tana tafe ne da bugun zuciyar Elhaj Sudais Uban masu gida, Tabas Rauda itace uwar gidan uban masu gida Murmushi ta sakarwa Rauda bayan ta mika mata ruwa mai sanyi ta sha tana sauke ajiyar zuciya Hafsat ta mikowa Rauda hannu ta ce" freind???? Rauda ta tsare hannun nata da kallo, freind fa, da wannan? Kawance? Hafsat ta ce" ki gane, ita rayuwa ba zaka ce kai zaka kare kai kadai ka ishi kanka komai ba, ina gayatarki kawance dan na kama maki da adu.a da shawarwari idan kin yarda da ni dan Allah ya magance maki damuwarki Rauda kam ta yi tsai ta fada tunani, shin ta aminta da kawancen wannan baiwar Allah wace take kanwa ga mijin da aka aura mata ko aa? Sudais na karban sakon Humaira, idannuwansa a lumshe ta rungumo shi ta gaba wajen kirjinsa ta cusa wuyanta cikin wuyansa , Wani doyi doyi na ruwan wanka wanda ke bayar da mugun doyi domin atach ne dadage a kan nata ga wanka da ya wajaba a kanta yau da gobe hakan yake saka mata kan na doyi Kansa ne ya ji ya sara masa, a hankali yake bude jajayen idannuwansa ya sauke a kanta, dan kwalin atampar nata ne ya fadi dan haka warin ya dake shi sosai Hannunda ya sa ya cireta daga jikinsa ya daga kafarsa da kyar dan ya koma bayi ya kuma yin wanka ya tafi , sai dai ta kara rike shi tana kokarin kuma like masa a jiki Cikin karaji ya ce" get out of my room! ( sorry fa za ina saka freinch, turancin nawa ba cancan bane🤦‍♀🤦‍♀🤦‍♀) Da sauri ta ja baya kirjinta na dukan tara tara dan tsoro domin ya rikide mata wani kala Da gudu gudu ta ja dan kwalin nata ta nufi kofa ta bude da mugun sauri ta yi dakinta wanda Samir dake zaune ya rakata da kallo, ba Hafsat din, ba Sudais din. Ba .sannan ga hajia matar oga ta fito tamakr an biyota da gudu...... Girgiza kai ya yi ya kuma buga number Oga Sudais bayan ya yiwa humaira tsawarnan ya ji juya na dibansa, kamar da wasa ya tafi luuuuuuuuii ya fadi nan wajen bed dinsa domin kwatakwata jikinsa ba karfi sannan tamkar ana zare masa laka, Idannuwansa yake sonbudewa tun karfinsa yake kokawa dan bude idannuwan nasa dan da ya lumshe su ita yake gani daidai inda ya cire mata hijab, da tsugunnin da ta yi da kuma mikewar da ta yi ta fice da gudu aman ya kasa , da karfi ya dago hannunsa na dama ya shiga dukan gefen zuciyarsa a fili yake ayanna inalilahi wa.ina ilaihi raj.une, ya Allah na tuba walahi kaina ba zai iya dauka ba, Ya Allah ka sanyaya min wannan damuwa tawa, Allah kana gannin halin da nake ciki, Ban aureta dan wani abin na jikinta , na aureta ne dan inai mata tsatataciyar soyaya... ya Allah yanda ka saka min kaunarta ta hana ni zama ka saka mata ya kasance ko ruwa zata sha sai ta tuno ni , Allah ta damu da ni, ta raine ni Dan nishi yake fitarwa dan kokari yake ya mike daga faduwar aman ya kasa bashi da karfin hakan, gaba daya karfin jikinsa ya fice A hankali jikinsa ya fara daukan zafi domin zafi da yawa ne ya hadun masa, Hakura ya yi da yinkurin tashin yana sauraron yanda wayarsa ke kuka , A fili ya kuma furta" *sonki kawai nake Rauda, ban aureki ba dan wannan.... koda kin kasance dumniya mai girma da kokarin saurin nuna ba zan shata ba sai ta nuna, (ko????🤔🤔) Daya daga cikin vigil din dake gadi a gidan mahaifan Sudais ne su Aisha suka tsatsare , Shima gannin yan mata masu kyai sai kwarkwasa suke ya saka ya biye masu domin suna irin haka yan mata na zuwa takanas dan su samu shiga su ga oga Sudais, wasu su ga gidansa , wasu neman nember wayarsA da sauransu a haka suke danfarar yan mata da yawa suna anfani da su ba biyan bukata domin su kansu basu da numbersa wace yake dagawa sai fixe Fuska ya yatsine yana nuna shima wani ne jin sai tambayoyi suke yi masa sai kace sun ajiye shi Aisha ta matso kusa da shi sosai ta ce" bawon Allah ko dai ya koma Saudiya ne? Na zo na zo ya fi a kirga wasu sun ce min yayi tafiya, wasu sun ce ya kaura, wasu aun ce yana wajen aiki , ka yi hakuri ka sanar mana inda yake dan girman Allah Haka kawai yake gannin wautar Aisha, shi yana mamakin zamani koda yake ba abin mamaki bane suniyar ce ta dawo haka, Cike da kufula ya ce" malama kun ga ku kara gaba, oga fa ya tashi daga nan iyayensa ke zaune a nan ya koma sabon gidansa a can GRA, sannan jita jita ana fadin ya auro wata yar sarki sun tare da tsoruwar matarsa Daga Sarah har Aisha mutuwar tsaye suka yi , Aisha ta dago da sauri ta ce"""" *❣IDAN KA RAINA INDA KAKE❣* Na: *SAJIDA* *_LITATAFAN MARUBUCIYAR_* *_Duk Karyar kada_* *_Yar Mahaukaciya_* *_Neman na kaina_* *_Bani da zabi_* *_Daga tafiya daukar soja_* *_Idan ka raina inda make_* *🌈KAINUWA WRITERS✍🏼 ASSOCIATION*🤝🏻 ```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}``` https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation 3⃣6⃣ *i.m sowi readers, babyna ke asibiti, yanzu ma na rubuta ne dan na isar da sakon, insha da an sake mu zakuna jina a kai a kai, muah ummu lallace💓* Daga Sarah har Aisha mutuwar tsaye suka yi, Aisha ta dago da sauri ta matsa kusa da Mutumin ta mika hannunta ta damko nasa a kidime domin ita ba ta wani ta taba namiji take ba ta ce" bawan Allah ka san kuwa wa nake nufi? Ina nufin Elhaj SUdais Uban Masu Gida wanda matarsa ta mutu yau kwana talatin da hudu, wanda matarsa daya kwal, Hannunsa ya janye da karfi domin har wani matse masa hannu take a kidime ya ce" kin ga, ki kama gabanki malama kin wani zo kon tsaya min a ka kina min zuba ke ba wani abin kika ban ba sai yawan magana kike sakani sannan idan aka yi katari Oga ya biyo gaishe da iyayensa ki jaza min fitina, ki kara gaba kawai Yana gama fadar haka ya juya da haushi haushin bai samu hadin kansu ba Sarah da ta fi Aisha jin bakin cikin wai Sudais yayi aure! Mutumin da tunda ta ji Aisha nada hanyar da zata ganshi ta makale mata dan kawai idan ta sadata da shi ta kwace mata shi sai kawai su tarar da mumunan labari wai yayi aure? Kuma wai yar gidan sarauta! Ta fi Aisha hawa, ta fita jin haushin wannan mumunan labarin dan haka ta juya rai bace ta shige motarta ba tare da ta tsaya ji daga Aisha ba ta nufi gidansu dan fadawa mamanta wani mugun abin murnar su ta koma ciki ko kuwa su kai maganar ga abanta shi ya bilowa lamarin ta hanyar da ya dace domin yana daukan kaya a kampanin Elhaj Sudais na shinkafar Niger Da mamaki Aisha ta bi motar da kallo, a pos dinta naira dari ne kacal wanda ta yi imanin ba za.a kaita gida a hakan ba sai dai bus, ita kuwa ta jima rabonta da hawa bos sai adaidaita ko motar Sarah aman yau ta yi tafiyarta dan ance Sudais yayi aure, lale Sarah tana tayata kishi har haka (sorry Aisha ) Da tashin hankali ta shige gidansu kamar yanda ta saba sai dai yau da kuka wiwi tana fadawa mahaifiyarta da ta taryota cewa wai Elhaj ya yi aure Daga bayi Aba ya fito buta a hannunsa na dama ya ja ya tsaya yana kallon Aisha, a kasan zuciyarsa yana tambayar kansa wanene wai Elhajin nan? Ganin Aba ya sa Aisha ta saki mama ta shige daki da dan gudunta Mama bata yi gigin bin bayanta ba domin har zuwa yanzu ba wani sake mata Malan yayi ba , yana dai kula ta yana fitar mata hakokinta dake kansa aman ba wani sake mata yake kamar da ba Ya jima nan kafin yake samun tsaftacecen wajen da yake alwalah ya zauna sosai ya yi alwalarsa cikin nutsuwa kafin yake mikewa ya fice a gidan Sai bayan fitarsa mama ta juya hankalinta ba a konce ba domin daman yanzu suka gama maganar ya barsu su je su ga Rauda da irin zaman da take ko ba ita mamar bama ko Aisha kadai ta je ta ganta aman ya murje idannuwansa ya saka bakin glass dan kar su ga fuska ya furta kalmar aa a barta ta kontar da hankalinta ta gina rayuwar aurenta idan ya ga da hali sai su je Labulen dakin ta dage ta shiga ta tarar Aisha sai kai kawo take ta hada zufa tana yarfe hannunta ta babarza gashin kanta du sun bazu tamkar sabon kamu A hankali ta samu ta kamo hannunta ta zaunar da ita bakin katifarta Hannayenta gaba daya biyun ta rike ta ce" ki nutsu Aishana , dan Allah ki nutsu Aisha ta dan yo tsai tana kallon mamanta, Mama ta ce" Aisha, suniyar nan na dawo daga rakiyarta tun lokacin da na ga Malan mutumin da du irin badalar da nake kirba masa sai dai ya kawar da kansa bai taba koda yi min ihu ba aman ya daga hannunsa ya sharara min mari tsoro ya kamani, tabas ko waye kai ka yi anfani da damarka, ka riki lokacin da Allah ya ara maka na zama tauraro ko wanda yake fada a ji ka aikatawa rayuwarka da kanka abin alkhairi tun kafin damar ta kubuce maka ka dawo kana bin mutane suna gudunka suna kyankyaminka Wannan bawan Allah Aisha bai ma san da kina doron duniya ba a sanina , Aisha ta wurgowa mama wani kallo aman bata ce komai ba ta ci gaba da kallonta Mama ta ce" Aisha, me zai hana ki bar maganarsa ki saurari manema auren ki , ki yi aurenki ki yi tafiyarki kema gidan mijinki ki adana kanki ki adana rayuwar ki? Aisha ta yi wani dan iskan murmushi ta ce" mama, baki gane mai nake nufi ba kennan? Wa cikin samarin nawa kike nufi? Balarabe mai gidan mai kwaya daya tak? Shamsu mai shagon atampa kwaya daya kwalin kwal? Ishak mai siyar da kayan mak up kawai? Ko kamalu dan makaranta? A cikin wa.inda na zana maki wa kike hangen zai gina maku tankamemen gida ya siy maku motoci ku iyayena mutanen da basu wanke nasu iyayen bama suna karkashinsu har yanzu bale a hango nawa? Ni kuwa fa? Sai kawai su zo su aureni a kaini a kimshe a daki , ba wani nishadin rayuwa sai daga gida sai gida mafarkin bai zama gaskiya ba? Haka kike so na kare a yawo a motar haya kamar yanda kike fama? Mama ta sauke ajiyar zuciya bata karaya ba ta kuma rike hannayen Aisha tana dan masagin irin ta yarda da maganarta din nan ta ce" Aisha believe me da kadan ake baba, dadaya ne zaki ga sun taso cikin kudi sun haye da kudi, da yawa kudin nan mai firgitarwa ana yin su ne daga baya Sai fa ki ga kin auri mai mugun kudin ya dawo ya talauce, kuma ki auri talakan kun zama hamshakai abin kwatance, shi Allah ba.ai masa wayo, yana yin abinsa ne bisa tsarin yanda ya hukunta Ki yi hakuri da Sudai.... Kafin mama ta kare maganarta Aisha ta mike da karfinta ta fizge hannunta , Kanta ta dafe da hannunta na dama kafin cikin daga murya tamkar tanaiwa kanwarta fada ta ce" haba mama haba mama haba mama, ina biye da ke a tunanina ke din mai sona ce ashe ba haka ba? To mama bara ki ji ni Aisha ko da ruwan balaki sai na auri Sudais domin da shi na dace da zama a gidansa na dace ba wai wasu masu kamo nan hada da nan ba! Har ta juya zata fita ta dawo wajen mama da ta saki baki da hanci zuciyarta na wani irin dokawa ta ja tunga kusa da ita ta rage murya ta ce" mama, kwarai mai kusi yana talaucewa Aman ba Sudais Mijina ba! Juyawa ta yi ta fice a dakin Mama ta kai minti goma na banza tana tunani, dumi ta ji a kuncinta tana lalubawa ta ji hawaye ne, a fili ta furta" wace irin tarbiya na baki Aisha? Wani irin halaya na nuna a gaban idannuwan ki? Tun yaushe na kashe ki da nunin kudi ya fi komai mahinmanci a rayuwa, Aisha Allah fa? Ya Allah ka kiyashe yayana da nadamar rayuwa, ka shiryar min da yarana ka basu dangana ga abin duniya, ya Allah ka yafe min kurakuran da na tafka a rayuwa ka bani ikon yiwa mijina biyaya , ka sanyaya zuciyarsa ya dawo min Ahmad dina Ta jima kafin take share hawayenta ta mike ta yaye zanin katifar Aisha ta fito ta hada a kayan wankinta Aunty mahaifiyar Sarah yayar mama wato nana Mariama ce ke kai kawo , can ta lailayo ashar ta afka ta juyo wajen Sarah ta ce" ke dan ubanki du fitar nan da kike, na kai zuciyata nesa na barki da yarinyar nan yar matsiyaci kina yawo dan ki bigi bakinta ki damo yanda zamu samu shiga wajen mai gidan abanki domin ci gaban mu ne gaba dayanmu ke ki aure shi ki zame masa fitilar gidansa sannan uwar yayansa , daga ni har ke Elhaj (wato mahaiffinta) ya daukaka martarbar mu mu yiwa yan bakin cikin mu nisa aman dan iskanci ki shigo min kina tayar da kura ki fdan yayi aure? Na rantse maki ko da boka ko da malan ko da balaki sai ya aure ki, ke ko matansa hudu ba wai biyu kacal ba sai fa ya aureki idan kin shiga mu fitar da sauran Sarah dake zaune hankalinta konce ta ce" mom na san sai kin kwato min wannan man din, ki gane ko ba maganar kudin ba man din yana ja, yana kawo fire.... mom idan ina shakar numfashi daya da yar yar uwarki ji nake tamkar na shaketa ta mutu, du na bata suturuna dan kar a ganmu tare kawayena su raina ni, aman a gaskiya na kagauta a yi a yo min auren nan da Elhaj baba na ware na bar banza da karnin talauci Murmushi aunty ta yi ta guada kanta ta ce" barsu da ni suke magana, haka muka taso da banzar yarinyar nan dan tana da farfadiya kin ga yanda su momy ke sonta suna riritata, sai da na samu na cucusa masu mumunan ra.ayi a kan son kudin su sannan na hada da na malamai suka yi mata korar kare, aman yanzu haka bokana ya fadan in dai mama ta ganta ido da ido to fa soyayar da take mata zata tashi ta fi da aman idan maganarta ne aka yi mata sai ta ji ba wanda ta tsana kamarta duniya, ahi ya sa ko waya muke da momy bana bari ta ji muryarta kanta dan kuwa some somen hauka zubar da yawu Haka ta yi ta banbaminta tana aibata Nana mariama da iyalanta sannan tana kara jadadawa Sarah haka zasu yi ta shiga jikinta har su samj biyan bukata (To fa) Wasa wasa sai da sudai ya yi jinyar kwana uku cir ko falonsa baya fita, Jinya ne yake na abu biyu zuciyarsa da rashin natsuwarsa Du Sudais ya yi laushi, burinsa ya ga koda wulginta ne aman matsalar bai saka cctv a gidansa ba bangaren da matansa suke sai a can bangarensa kawai na siri , bai saka bane dan baya son shiga rayuwar matansa, yana fadi cewar kowa nada siri a rayuwa, in dan gudun wani abin ne Allah na tsare su sannan shi kamsa Allah na tsare shi sai kuma irin matakan tsaron da ya saka na zamani harda dakin da idan aka shiga bindiga bata ratsa kofar, kai ko bom sai wace ta amsa sunanta ba karama ba da zata dan yi busssss ta dan tsoratar , Aman a yau sai yake jin haushin rashin sakawar da bai yi ba, harma ya dauki aniyar sai ya saka a dakunansu ko dan ya ringa gannin shigarta da fitarta Shiryawa yake a yau cikin suit, ya saka farar rigar ya bala boturanta saman wando ash kala mai santsin gaske mai duhu ya mugun yi masa kyau Kum dinsa ya dauka ya caje sumarsa yana ayana sai ya yi gayaran fuska domin yau kwanansa shida bai gyara fuskarsa ba ya rage gashin kansa Rigar saman ya dauko ya rike a hannunsa bayan ya saka cravate din aman bai matseta ba ya dan sasautata sosai daidai botiran rigarsa kwaya biyu da ya bari Agogon hannunsa ya duba karfe tara , a yau yana son zuwa aiki ya yi aiki sosai sannan yana son yin magana da Samir, aman yana gannin maganar zai fara yi da samir din Yana gamawa ya dauko yar karamar jakar computersa kampanin hp wace a cikinta ya saka kys dinsa da waya kwaya daya yar karama subulbula mai suna samsung fara kar da ita Gaba daya sauran wayoyinsa ya bari a nan dan baya son takura Yana shirin fita Humaira na shigowa ta karaso ta dafa gefen wuyansa ta ce" honey har ka samu karfin zuwa aiki? Sudais ya lumshe idannuwansa wa Humaira, a hankali ya dan janyeta a jikinsa ya kauce ya fice ya barta nan tsaye domin ko a daren jiya yana mu.amala da ita ne yana dane ciwon cikin dake murdarsa sanadiyar warin nan dake damun hancinsa wanda mamaki take bashi irin yanda ita baya damunta, da fada da komai ya samu yar nustuwa ta hanyar zubar da wahalar da ta kara dadabe masa mara Da harara ta bi bayansa ta watsa hannayenta ta yi dakin wajen da yake ajiyar kudi ta bude ta kwaso dan tana so ta aikawa mamanta a kasan zuciyarta kuwa tana ayana zaka gama fushin ne , ni din dai ni zaka dawowa dan na san abinda ka dorawa kanka na baka hulda da macen da bata kai mizanin shekara ashirin da shida zuwa sama ba, wannan yar shilar taka sai dai ta gaji ta kama gabanta banza da ita Sudais na fitowa Samir ya karaso da sauri ya karbi jakar hannunsa yana gaishe shi da tambayarsa saukin jiki A takaice Sudais ya amsa shi da " Alhamdulilah Tafe suke Sudais na zaune gefwn direba Samir kuwa na tuki shiru cikin motar sai uban sanyin ac dake tashi Sudais murya a dake kamar yanda ya saba ya ce" ka dakata mu sha caputulo Samir ya amsa da " an gama Wani makeken restaurant ne na masu hannu da shuni, nan samir ya kai motar su gefwn wajen park ya tsayar da motar suka fito Idan ka gansu sai ka yi tsamanin abokai ne domin Samir ma sabon jini ne mai san kama kansa , sosai ya iya gayu da hade fuska idan hakan ya taso Sudais kuwa tafe yake cikin tafiyarsa ta kakarfen namiji, sai ka ce irin turawan nan masu shegen karfi domin a yau irin shigarsu yayi Wajen kujerar ya ja zai zauna ya dan bale botun din rigar costume din tasa na tsakiya wanda daman shi kadai ne ya saka ya zauna inda Samir ya yi commander din abincin ya ja shima ya zauna Sudais ya tsare samir da kallo tamkar juju na karewa mai laifi kallo dan ya ingiza shi ya fadi gaskiya Wannan kallon du ya saka samir A uku, damuwa karara a fuskarsa da tsoro domin Sudais bai taba yi masa irin kallon ba, shi ya kasa samun nustuwa sai dan mutsu mutsu yake yana dan dagowa ya kali Sudais ya sada kansa kasa *Me kace sai na yi?* Sudais ya jefowa Samir tambaya a dake ba tare da ya bashi kofar gane me yake nufi ba Nan da nan zufa ya fara karyowa samir, ya dan gyara rigar shadar jikinsa a ransa yana ayana ni na san ba banza ba , domin a kampani ba irin cafe din da babu aman Wai oga ya bada umarnin su tsaya a gefen titi su sha caputilo? Muryar samir rawa ta fara, shi yana jin haushin irin yanda Sudais ke yi masa kwarjini aman yana danganta haka da irin yanda Sudais din ke da kwar jini , da kamala Samir ya ce" oooooga ban fahimci maganar ba Sudais ya kawar da kansa ya ce" ina so ka fada min etape par etape yanda zan bi na karkato tunaninta kaina, ta so ni, Samir rayuwana ne ke tangalgal tamkar ruwa a kan bokici a kan yara, ban zauna na koyi karatun soyaya ba , ban san ta ina zan fara ba, ban iya bin mata ba, damuwar *RAUDA NA TAFIYA DA BUGUN NUMFASHINA, NA LURA IDAN NA YI SAKE LUMFASHINA NA IYA DAUKEWA A CIKIN YAN DAKIKUN DA BA WANDA ZAI ANKARA BALE YA KAWO MIN DAUKI, SAMIR KA SAKA NI A HANYA NA GANE MATATA* da mamaki, da tausayi Samir ke kallon Sudais,, lale ya yarda *So mugun wasa ne*, ya yarda *So guba ne*, kuma ya yarda *So sarki ne*, a gaskiya sai da ya dago ya karewa Sudais kallo, a ransa ya ayana ELHAJ SUDAIS UBAN MASU GIDA!, ya zama bashi da karfi bale dabara a gaban yar cininiyar yarinya Kansa ya sada, ya kuma dagowa daidai lokacin da aka kawo Caputulo 🤤 aka ajiye Cike da ilimi Samir ya dauki papier ya yaga ya dan goge bakinsa da hannayensa biyu sannan ya yiwa Sudais nuni da hanayensa da idannuwansa kan ya dauka mana Sudais ya hade rai ya yi masa kallon karfa ka raina ni, Gannin haka ya samir dam ya ajiye nasa ya gyara zamansa ya ce" oga, ka yi hakuri da abinda zan fada, na farko dai dole, dole, dole sai ka ajiye abinda ke sakawa tana jin tsoronka, wanda kai ka dauke shi a matsayin ba komai ba ..... sai dai wannan shi ne damuwar Ba tare da Sudais ya kali samir ba ya ce" me ne!? Samir ya ce"""""""" *❣IDAN KA RAINA INDA KAKE❣* Na: *SAJIDA* *_LITATAFAN MARUBUCIYAR_* *_Duk Karyar kada_* *_Yar Mahaukaciya_* *_Neman na kaina_* *_Bani da zabi_* *_Daga tafiya daukar soja_* *_Idan ka raina inda make_* *🌈KAINUWA WRITERS✍🏼 ASSOCIATION*🤝🏻 ```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}``` https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation 3⃣7⃣ Samir kai tsaye ya ce" tsare gida, girman kai, da wannan abin wai sai ta ce tana sonka a farko Sudais ya zaro idannuwansa, ya cije lebensa kafin yake saki ya nuna kansa da yatsa daya ya ce" Samir, ni ne mai girman kan? Samir ya dan dago yana kallonsa, dan daburcewa yayi ya dan ja kujerarsa nesa da sudais kadan yana dan sine kansa dan kar ya kai masa bugu Sudais ya yi dan murmushi ya ce" karka damu , ci gaba ai ni na tambayeka Samir ya sauke ajiyar zuciya ya ce" oga, ka gane, mata fa akoy masu aji...., akoy matan da suka san kansu, suke kare mutuncin kansu, wa.inda kudin mutun ko kyansa ba zai saka su saki layi ba , bayan wannan ga irin matsalolin dake tsakanin Hajia (wato Rauda ) da kuma kai, wa.inda ita idan baka yi da gaske ba su ne hujojinta na gudunka a rayuwa, Sannan sai ka kai zuciyarka nesa ya kasance ka sadako ka sauke kanka ka isar mata da sakonka ta hanyoyi daban daban, Sudais ya tsare Samir da ido, a ransa yake ayanna wato shi wannan kamar ma mai jin haushina, sai kace wanda yake jiran irin hakan ya wankeni, uhum aman ba komai na tabata shi iyakar hakan ne kuma yanda ya fadan na tabata Samir mai kareni ne a waje ba dai ya hadu da wasun masu yi min muguwar fasara ba, to aman me yake nufi? Ni na sada kaina na bi ta, Dan murmushi yayi wanda har Ya sa Samir sauke ajiyar zuciya domin a tsorace yake da Sudais, Sudai bai ce komai ba kuma bai sha caputulon ba ya mike ya dauki rigarsa dake rataye ya yi wajen mota Da sauri samir ya bada carte dinsa suka saka suka cire kudin caputulon suka mika masa shima ya bi bayan Sudais ba gare da ya sha Caputulonsa ba😟 Haka suka karaso wajen aiki wanda suna shiga aka fara tarbo sudais da takardu Murmushi yayi gannin Shuraim ya biyo shi siyen gold din, ya kawar da kansa ya yi nuni da yana zuwa Wani gold ne da aka kirarsa aka saudiya, A lokacin sai suka nunawa Sudais da Shuraim shima gagarumin dan kasuwa ne Sai ya dandajar da abin ya yi tayin da basu so ba dan haka suka salamawa Sudais Sai dai matarsa ta tayar da kafar baya, kin san larabawa da matan su, ta tayar da bali domin ta gansa a shagon Sudais na Nigeria cikin tala zee aflam, sarka ne da yan kunaye ba masu wani girma ba kawai kirar ne aka yi ta yan gayu aka zuba zunzurutun kudi Tana gani ta ji ai kawai tana so shine ta tayar masa da hankali sai da yayi tafiya gari ya gari ya zo domin Sudais kin daga wayarsa ya yi dan Shuraim akoy kyamar du mutumin da ba balarabe ba, wannan ya sa basa hayewa juna da Sudais domin shi kuwa yace ba zai je yanai masa fadanci ba kowa yana neman na kansa dan haka kowa yayi iko da nasa... idan sun hadu ma sai dai su gaisa daga haka ba wani abin dake shiga tsakanin su Sudais na zama a office dinsa Basma ta nemi izinin shiga ya bata Tana zuwa ta gaishe shi kafin take gabatar masa da bakin da sukai na kasashe uku a safiyar yau kuma du sun zo ne a kan wannan gold din Sudais ya yi tsai yana sauraronta, Sai da ta gama ya lumshe idannuwansa bai bata amsa ba kuma bai salameta ba, Wayarsa ya dauka yar karamar wace ke dauke da numbobin manyan mutanensa Sakawa ya yi ya buga kira Har kasar Saudiya Tana ringin na uku aka daga daga dayan bangaren akai masa salama irin ta adinin musulunci bayan ya amsa mutumin cikin yaren inglish ya ce" ogan mu Sudais ya dan saki murmushi yace" wane ni, ai kaine oga Mutumin ya ce" na baka, a gaskiya kaine oga, wai da gaske zaka fara harkar gawayi? Sudais ya yi murmushi ya ce" har na yi nisa a ciki Mutumin ya ce" masha Allah , mutumina ka fa fi da fasowa, Allah ya taimaka ya kuma kare ka Sudais ya amsa da " amin mai gidan mu A tare sukai murmushi, Sudais ya dan ja numfashi ya ce" Brahim, wannan sarkar zan samu wata ne irinta? Brahim ya ce" Sudais, sarkar nan ta fito ne a matsayin irin kayan da idan muka yi kwaya daya bama sake irinsu, ku kuka fitar da tsarinku cewar orin kirarku unique kuke so, ai Shiraim kansa ya dawo da matarsa wai irinta yake so, har sai da ya dora min kudin sosai na nuna masa da ina irin haka da ban yi nisa har haka ba, amana daya ce, ni na yi alkawarin du wanda na dauki alkawari da shi ba zan ci amanarsa ta hanyar baiwa wani kirarsa, komin girman kudin da zai ninka min Sudais ya dan juya saman kujerarsa yana sauraron bayanan Brahim, can sukai salama Kurawa takardun gabansa ido yayi, kowane da irin kudin da ya baiwa sarkar, kowane kuwa ya bada jibgegen kudi na mamaki, Murmushi ya yi ya mike ya cire rigar nasa ta sama ya ajiye a nan ya yi gaba Basma ta dauko takardun ta bi bayansa Bangaren gold gold din ya nufa, Yana shiga ya shiga can wajen coffre din ya dora babar yatsarsa ta dama wace dole sai da ita zai budu Yana buduwa ma wani glas ne da wajen code shima, Gani na yi ya daidaita idonsa na dama abin ya yi wani zuzuzut ya bude, Zo ka ga sakin baki wajen yar mutan Niger, ya wannan sarka a rataye a jikin wani wuya na mace haka, sai daukan ido take ba wani dabkekiya bace kawai tsaruwa da kyau Bayansa ya waiwaiya ya ga suna tsaye, da Shuraim, da Frank dan america wanda shi zai kai fada ne, sai mace NADIYA uar kasuwa ce ta zo ne siyanwa yar gidan shugaban kasa wace za.ai aurenta sannan kowane sai da ya fadi ga abinda zai yi da ita dan kowa a wajensa an nuna ana sonta sosai Mirmushi ya sakar masu sannan ya karaso inda mataimakinsa, da sairan ma.aikatan da suke kula da bangaren du sun halara a wajen sai Basma dake rike da takardun tana kara karanto masa cikin kwararen turancinta Sai da ya gama sauraro ya mika hannunsa ta miko masa da sauri A hankali ya kara takawa gabansu, kowane sai ya duba da kyau ya jinjina kai sai ya mika masa takardarsa Har ya zo kan Shuraim, wanda shima ya amsa suna kalon sa Dan murmushin ya sakar masu ya ce" i.m sorry ba na siyarwa bane A tare suka zaro ido, Nadiya ta fara magana ta ce" Uban masu gida, ka kayide mana kudinsa yanda kake so mu saya cikin mu wanda yake iyawa sai ya siya Sudais ya maida kalonsa kanta ya yi mata kallo daya ya kawar da kansa, Shuraim ya ce" SUDAIS ka taimaka ka siyar min da sarkar nan, ka dai san a tare akai mana talarsa ban san zata birge matata ba sai yanzu, ko abinci bata ci ka taimaka min na je mata da ita Shima kallonsa sUdais ya yi bai bashi amsa ba, Frank ya ce" SUDAIS , kar ka yi zabunta ka siyarwa wa.inda suke adininka, na rigaye dukansu zuwa wajennan sannan ban yi tayin wulakanci ba, idan har kudin ne basu yi ba na linka maka su sau uku Kamar da wasa fama suke su tayar da yar hayaniya kowane yana kara kudi kan na dan uwansa Sudais ne ya yi masu salama cikin dan daga murya ko zai katse hayaniyar Dakatawa suka yi gaba dayansu suna kalonsa, Gilas din idonsa ya cire wanda hakan ya basu damar gannin kwayar idonsa, muryarsa a dake kamar yanda ya saba ya ce" i said ba na siyarwa bane, ban taba linka riba ba! Ba zan fara a kanku ba Yana gama fada ya juya da niyar tafiya domin yana da wani meeting din, Da sauri Shuraim ya riko hannunsa ya ce" aman idan ba saidawa bane me zaka yi da shi Sudais? Sudais ya bi hannunsa da ya rike nasa da kallo dan haka Shuraim ya yi gagawar cikawa yana kalonsa , Sudais ya dan gyara wajen ba tare da ya bashi amsa ba ya yi ficewarsa a wajen Kowane dai da bacin rai ya bar wajen suna ayana daman shi haka yake sai ya ga dama yake sakewa idan ya ki sai ya daure tamkar wani kurma Da yama kamar kulun Samir ya tuko Sudais a mahaukaciyar motarsa wace ba a ita suka je office ba canzota ne suka yi , hakan suke ko yana cikin bada kama ko me shi dai ya san dalilinsa na yin hakan Samir na biye a bayansa har falo da wata jaka wannan karon wace ba da ita ya fita ba bayan ta laptop dinsa Faman zama suke sai hayaniyar su Rauda da hafsat ta saka Sudais ya yi gagawar kallon wajen kicin din, Jin kakaniyar ta gaske ce ya saka shi dagawa Samir hannu alamar bye, shi kuwa ya nufi Kicin din gabansa na dukan dari dari Ja yayi ya tsaya ya harde hannayensa ya zuba mata iso, Sun bada baya ne wajen Fur suna kara decoration din cake din da suke yi dan murnar zagayowar ranar haihuwar Rauda wace tunda suka tashi suke dan kakayniyarsu fuskokinsu kuwa du sun dan shashafawa juna suna ta dariya abinsu da alama dai Rauda ta mugun sakin jikinta da Hafsat Wando ne dogo baki slim wanda yake dan kyalkyali ya kameta sosai sannan yana bin yanda cinyoyinta ke rawa da bayanta ko ya ta motsa sai riga mai dan tsayi har daidai gwuiya daga baya daga gaba kuwa ta dan dara cibinta kadan wace itama bata da nauyi ko kadan sai likewa take a Jikin Rauda ko ya ta juya Kanta kuwa ta daure gashin sai ta dora wata bakar hula mai tiloli ta rufe gashin gaba daya sai na gaban goshinta da yayi lufluf da na bayan wuyanta Hafsat kuwa doguwar riga ce a jikinta sai hula itama sannan sun jona wayar Hafsat a gefe sun saka waka a karamin sauti tana dan tashi ana ta waka "it's my birthday ........ har dan juyi suke ana dariya ana hada cacadeden cake Ajiyar zuciyar da bai san ko na meye ba ya shiga jerawa, sai kuma ya fara ji iska ta yiwa hancinsa kadan yana kokarin shidewa domin kuwa Rauda tana dan rawar nan ne tana dan jujuya abinnan wanda ita ba da gangan take yi ba, idan dai ta juya suma sai sun juya Hafsat ce ta juyo dan daukan abin matsa cream din ta zuba su matsawa cake din ta ga Sudais tsaye ya cika kofar yana kalon su Bakinta ta bude da niyar yi masa sannu da zuwa ya yi gagawar dora yatsarsa saman lebensa sannan da idannuwansa ya yi mata gargadi kan kar ta yarda A hankali ya juya ya fice a kicin din ya dauki kayansa ya nufi dakinsa, Yana shiga ya fada saman doguwar kujerarsa, lumshe idannuwansa yayi yana hangenta, a hankali ya bude idannuwansa ya kai dubansa wajen bayi, shi kadai ya saki murmushi sannan ya mike ya nufi bayi dan shirin zuwa mosque Haka su Rauda suka sha shirmen su a dakin Raudar suka ci cake din su sukai kallo , a takaice dai a gajiye Hafsat ta yi mata salama itama ta kuskure bakinta ta gabatar da sallar shafa.i da wutiri Tana cire hijabin tana nikewa tare da salayar ya shigo Wani irin mikewa Rauda ta yi, jikinta a lokacin ya dauki bari tama rasa yanda zata yi ta mayar da hijabin kan kayan dake jikinta Tsareta ya yi da kallon nan nasa mai tayar da tsikar jiki yana kara kusantota wanda daga shi har ita du taki daya idan ya yi sai gabansu ya fadi Saurin sada kanta ta yi kasa, tana damke rigar jikinta tana janta kasa kasa kadan kadan Kusancin da ba zai yiwu hannu ya ratsa tsakaninsu ba ya bari, wanda shima a hankali ya matso ya kasance kanta yana jikin fafadan kirjinsa Lumfashinta dake fita da sauri da sauri ne yake dukan kirjinsa wanda hakan ya hadasa masa kasala banda wanda yake ciki, Dan dukowa yayi ya kai hancinsa daidai wuyanta ya shaki kamshin wajen wanda har sai da ya yi dan hummmmmm dan kamshinta ya tafi da imaninsa, ba karni, ba warin ruwa na kai kamshi ne kawai take Da sauri ta yi kokarin dan ja da baya wanda ya yi saurin saka hannunsa na hagu ya rikota ya jawota ta hadu da jikinsa sosai A hankali ya dago hannunsa na dama ya fiyar da sarkar dake hannunsa ya daidaitata a wuyanta ya saka mata ya saketa ya bala mata sannan ya matsar da gashinta ya saka mata yan kunayen kafin yake maido mata gashin nata A hankali ya rabo fuskarsa da tata ya taho a nitse ya goga karan hancinsa da nata yana dan kara murzawa idannuwansa a lumshe Hakama nata wanda ita kanta bata san me ya sakata lumshe su ba sannan me ya hanata guduwa duda ya cikata Zuciyar ke fadin" sudais, cafko su, ka cafko su sudais, naka ne , halalinka ne sudais, ka cafki leben Rauda ka yi masu shan alewa mai shinke, ka tande su har sai sun yi jajajir, Wata kuwa ta hane shi cewar " haba sudais, Raudar nawa take? Ka barta ta gane karatunka tukunnan, ka barta ta fada a tarkon da ka jima cikinsa kana iyo ya kasance itama ta kaunace shi har ta yi gudun fita a cikinsa, ka barta ta girma ta kara shekaru kan nata kafin ka nuna mata wannan hanyar Sudais, Kar ka tsorata Angel dinka Da alama dai shawarar nan ita ya dauka domin a hankali ya raba fuskarsa da na Rauda, ya dan ja baya yana kare mata kallo wanda har yanzu idonta a rufe yake ruf hawaye yana dan fita ta cikinsu Hannayenta cikin nasa ya kai daidai lebensa ya sumbace su a tatare lokaci guda sannan ya ce" *HAPPY BIRTHDAY KHALB* Da sauri ta buda idannuwanta wanda bata yi shirin bude su ba *KHALB* TA maimaita a kasan zuciyarta , daidai lokacin da maganarsa ta katseta ya ce" da ke ta dace, ta yi maki kyau......., Rauda, *ke ce mai kyau* , Yana gama fada ya matso ya bata peck a kunci ya cika hannayen nata ya juya ya fice Mutuwar tsaye ne Rauda ta yi, ta kusan minti talatin a haka ta kasa gane karatun Sudais, A hankali ta matsa kusa da madubi ta kali kanta a ciki, Idannuwa ta zaro gannin sarkar da ya bata, ni kaina idannuwan na zaro domin sarkar nan ce ta kampani ya bata ..... Humaira ce konce tana ta juyi ita da kawarta suna magana a whatsup, kawarya ta ce" lale ne hajiyata , na yarda oga yana mugun sonki, irin wannan kyauta haka? Sarkar gold haka? Aman odan kin siyar ba zai gane ba? Humaira ta yi murmushi ta ce" hum, ba wani ganewa da zai yi, wai ita amarya an kawota an jibge kawata ki tura ki ji nawa zasu saya na sayar na kashe wutar gabana na samu hanyar da zan kori wannan banzar cikon bencin! Kawarta ta ce" *❣IDAN KA RAINA INDA KAKE❣* Na: *SAJIDA* *_LITATAFAN MARUBUCIYAR_* *_Duk Karyar kada_* *_Yar Mahaukaciya_* *_Neman na kaina_* *_Bani da zabi_* *_Daga tafiya daukar soja_* *_Idan ka raina inda make_* *🌈KAINUWA WRITERS✍🏼 ASSOCIATION*🤝🏻 ```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}``` https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation 3⃣8⃣ Kawarta ta ce" ai ni nama yi mamaki hajiata, har ta tare du kina kallon ina sai kace baki faso ba? Bayan kina tare da yan bariki ya dace a ce aikatawan ne kawai da kika hana kanki bakya yi aman du sauran halayen mu bai dace ace kina yi ba, yanzu a irin yanda kike bamu labarin girman bulalar oga kika yarda wata banza ta shigo tana shan dukanta harma tana lashe amanta ! A gaskiya kin yi sakaci da yawa.... Humaira ta ce" ke bai fa taba hada shinfida da ita ba Kawarta ta ce" kin tabata zaki iya rantsewa da hakan? Humaira ta yi murmushi ta ce" zan iya bada rayuwana a matsayin wannan maganar, Elhajina bai je shinfidar banzar nan ba, na sani duda ina nuna gajiyawata aman yana ji da ni, ni din nan dai ni ake kira zuma mai harbi, dole sai da ni elhaj zai gyagije ya kwashi ruwa Kawarta ta ce" bana son wasa, ki kara hima...., bara na shigar da sarkar mu gani idan ta an yi mana tayin kirki sai na saka ki a hanyar da dan uwarta ba zata kara jima maki a gida ba Humaira ta yi murmushi ta ce" sai na ji ki Tana kashe wayar da Kawarta ta tabo mutumin da yake saida mata mai, wani inyamuri ne dake yi mata zazafan hadi, shi din da kansa ma shafa man yake domin idan ka ganshi tamkar zabaya du fatar ta cinye , Tana tabo shi ta fada masa ya hado mata zafafa zata je ta karbo Bayan nan ma oder ta yi na kayan kwaliya bayan du irin wa.inda take da su a dakin, ta kuma yi na atach (meche) Tana gamawa ta kuma dauko sarkar, itama gold ce tsantsareriyarta , itama ya sayota da tsadar gaske sai dai ita ba unique bace akoy irinta a can saudiyar , da ya ga zuciyarsa ta rikice kan sai Rauda ta saka wancen dan yayi adalci itama ya dauko mata wannan aman shine ko ado bata yi masa ya gani ba zata saida.......halayenta kennan mota kanta dan ba wanda zai yi gigin siyan motar da ta fito daga wajen Oga Sudais ne da ta siyar da motocinta ta tabata ba zai barta ba motar hawa ba ,...., kuma du wannan hadamar da take bata yi ginin gidan da za.a kala a ce lale wannan tana auren mai shi aa kudaden sun kare a siyen banza siyen wofi... atash du tsadarta bata gani zata cire ne ta saya ga rashin adano idan ta cire daga kanta sai dai ta zubar Da mugun tsoro Rauda ta zaro ido, da sauri ta cire sarkar daga wuyanta ta zauna bakin gado tana kallo Tambayar kanta take mene haka? Me ya sa ya yi mata irin wannan kyautar? Sudais ne Rauda.. Da sauri ta mike ta saka hijabinta ta fito ta nufi dakin Hafsat Hafsat dake zaune tana yanke akaifunta tana kallon wayarta kira ne ta shigowa sai dai ta yi murmushi ta ki dagawa Whatsupp ya koma ya rubuto" aa fa, Hafsana a rangontawa zuciyana idan ba haka ba na yi sabko gidan nan sai dai oga ya harbe ni, na zo na gan ki Hafsa, ki yi hakuri ko dan dago hannu ne ki yi min kar zafin ya yi min yawa ga na oga ga naki Murmushi ta saki bayan ta karanta ta ki yi masa replay, a fili ta furta" lalema yayan nawa ne mai hada maka zafi SAMIR? Dago kanta ta yi tana amsa salamar Rauda wace ta nufota da dan sauri ta zauna tana miko mata sarkar hannunta ta karkata kai tana ciro yan kunayen ta mikawa Hafsat Idannuwa Hafsat ta zaro, tabas ta san sarkar nan , Dago da kanta ta yi ta kali Rauda ta ce" Sis?? Rauda ta samu waje gefen bed din ta zauna itama, murya a dan raunane ta ce" ana kyauta ne wa masoyi, wannan kyauta ne irin na masoya, sis wace ni ? Na tabata dan ya fita a hakina ya bani sarkar nan dan ya baiwa matarsa, ki yi hakuri yayanki ne aman kuma gaskiya ce... da bakinsa ya furtan kalmar kiyaya,! Ke bama wannan ba dalilina na kin komai nasa mai karfin gaske ne Hafsat da ta saki baki tana kallon Rauda, a ranta take ayanna anya kuwa rauda zata yi wayo? Tana fadin haka wa ni kanwar mijinta🤔, Kawar da hakan ta yi ta ce" sister kin san da sarkar nan Gold ne? Zaro ido Rauda ta yi harda mikewa da sauri tana kallon Hafsat Murmushi Hafsat ta yi ta kamo hannunta ta zaunar da ita kusa da ita sosai, Ta ce" wani lokacin ba.a anfani da abinda mutun zai fada Rauda, ki kasance babar mace wace ta san kanta mana, a duk lokacin da yaya zai fada maki mumunar kalma ki yi analysen ta, ki koyi karantar abinda ke zuciyarsa koda yana cikin bacin rai ne Rauda, sannan wannan kyauta mijinki ya yi maki, koda bakya sonsa kamar yanda kike ikirari... koda kina da abinda ya hana ki sakewa da shi wanda kika ki fada min ko menene wannan sarkar taki ce, halalinki ne, ki adana abinki Ajiyar zuciya ta sauke ta ce" Hafsat, a ina na samu damar karantar abinda ke cikin zuciyar mutumin da yayata ke masifar so tamkar ranta? A kansa Aunty Aisha na ikirarin sai ta halaka mutun, a kansa ta yi rantsuwar sai ta bata da kowa! Ido Hafsat ta zaro, a fili ta furta" What? Kina nufin yayarki ce ke son Yaya? Rauda ta yi kiftkift da ido, ta kalli hafsat, lalle ta san ba subutar baki ta yi ba domin Hafsat tana nuna mata kauna ta gaskiya, to aman Aisha kuwa yayarta ce fa, sai dai abu guda da take gannin kamar ta yi saurin yi shi ne irin sabo da shakuwar da ta shiga tsakaninsu da Hafsat ko dan bata samu haka da Aisha ba? Kulun Aisha cikin hantararta take da dizgata Hafsat ce ta kamo hannayenta ta ce" fada min sister, ko baki yarda da ni bane? Rauda ta sauke ajiyar zuciya ta ce" tun ranar da muka je gidanku wajen birthday aunty ta kamu da matsananciyar kaunar Elhaj Sudais Du abinda ya shafe shi bata yi masa rikon Wasa, dalilin an canzata a wajen aiki kusa da shi sai da na ga wulakanci iri iri, Ban san wannan auren da me zan kwatanta maki yanda ya diro min ba a lokacin da na gane cewar shi abanna ya bani a masalaci, walahi abinda ya hana zuciyata tsayawa kawai nisan kwana ne..... na girgiza a ranar , har yanzu ko baci nake abinnan ya fado min a rai nakan farka ne da mugun zazabi da tsorom kowa Hafsat ki duba ki ganni da wane zan ji? Da Aunty Aisha? Da matarsa? Ko kuwa da shi din kansa wanda ya kiraye ni da matar sadaka , tsohuwar mace, ya furtan cewa ya tsane ni, da wane zan ji? Hafsat tana sauraronta tana murmushi a kasan zuciyarta, wato ita nan gani take idan ya saka mata soyayarsa a zuciyarta har ta isa ta kwaci kanta, shima yaya wani abu ne da shi ko mai yasa ya furta mata kalmar kiyaya? Sai kuma abinda ya birgeta maganar yaya ta yi mata ciwo dan kuwa gashi har tana nisawa, hannun Rauda ta kara rikewa ta ce" kina nufin dai ya sawake maki ya auri yayarki? Rauda ta sada kanta ta yi zuru, can ta dago ta ce" eh, ai ba wani abinda ya......... kuma sai ta yi shiru ta janye hannunta tana dan murzawa Hafsat a ranta ta ayanna kin makaro matar yaya, A fili kuwa ta ce" Allah ya zaba abinda ya fi alkhairi Rauda ta cuno bakinta tana amsawa da amin ta mike da niyar tafiya dakinta Hafsat ta tsayar da ita ta ce" ga sarkar ki Rauda ta ce" ki ajiye min a wajenki plz Hafsat ta zaro ido ta girgiza kai ta ce " ko daya, ki je ki ajiye a wajenki na roke ki, sannan ki tabata kin tashi da wuri dan mu kimtsa abubuwan da zamu tafi gidan su Momy kin ga jibi ne adu.ar 40 din Marigayiya Rauda ta amsa jiki a sanyaye ta juya ta fice a dakin Hafsat Washe gari ya kama da dan wuri wuri suka shiga kimtsawa Hafsat ta sakawa Rauda kaya kala biyu a jaka da turare da sauransu, Da yake kwana aka yi ana saukar alkur.ani a can baban gidan an kawo abincin sadaka da aka yi dan haka Hafsat ta ibar masu suka ci suka fara shirin tafiya a lokacin har karfe uku na yama ya yi Basu ga wulgin Sudais ba domin tun da safe ya tafi can gidan yana tsaye dan gannin an yi komai yanda ya dace tunba fannin malaman da suka zo gari da gari suna bayar da gudunmuwarsu wa wannan marigayiya da ahalinta (masha Allah, kowa halinsa ke binsa) Karfe biyar na yama suka gama shiryawa, ba wani kwaliya suka yi ba Rauda ta saka dogon hijabinta ja mai hanaye wanda gaban goshin yana da kamar abin dauri ya kama fuskarta ya yi mata kyau sosai Ba kwaliya a fuskarta ko kwali bata saka ba hakama hafsat suka fito Direba musa ne ya zo da sauri ya gyara mota yana gaishe su bayan ya karbi jakar kayansu ya saka a bayan mota suka shiga ya ja Hafsat tana jin haushin Humaira ko tace mata ta tafi , kwata kwata bata yi mata magana wai dan tana kula Rauda Mota na tsayawa Rauda ta riko hannun Hafsat sanadiyar gabanta da ta ji ya yi wata mahaukaciyar faduwa sakamakon ganinsa da ta yi yana tsaye suna gaisawa da wani baban mutun mai cike da kamala Gabanta yake mugun bugawa bilhaki, sai da Hafsat ta kaleta da kyau tana tambayarta lafiya kafin take kamo adu.a a zuciyarta har ta fara samun nutsuwa Yar kwallah ce ta ji ta tarun mata a idannuwanta , a hankali ta bude gefenta ta fito ta tardo Hafsat wace ke nanata mata ta kontar da hankalinta ba abinda zai faru Ta dan nesa da shi suka zo suka gita wanda ya tsareta da kallon nasa mai sakata ta rikice , tambayar kansa yake ina nikaf dinta ne? Shi hijabinma sai yake gannin kamar ya yi mata kadan , kallon dai du na kishin mazan dake dan zirga zirga kan baki da ma.aikatan gidan da kuma yan uwan marigayiyar Hafsat ce gaba Rauda a bayanta suka yi salama cikin tankamemen falon Momy wanda ya tara kima kiman baki, tun daga kan mutanen momy , jama.ar marigayiya, yan uwa da abokan arzikin., sai kawayen Humaira suma suna zaune suna yar hirarsu, Dif falon yayi shiru tamkar an ce su juyo du suka juyo suka zubawa su Rauda ido da kallon da ita ba zata iya fasara irin girman kiyayar da take hangowa a idannuwan mafi yawancin mutanen Momy ce ta mike rai bace ta nufo su ta.... *❣IDAN KA RAINA INDA KAKE❣* Na: *SAJIDA* *_LITATAFAN MARUBUCIYAR_* *_Duk Karyar kada_* *_Yar Mahaukaciya_* *_Neman na kaina_* *_Bani da zabi_* *_Daga tafiya daukar soja_* *_Idan ka raina inda make_* *🌈KAINUWA WRITERS✍🏼 ASSOCIATION*🤝🏻 ```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}``` https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation 3⃣9⃣ *SAKON GAISUWA GAREKI MA CHERIE TUN DAGA FRANCE WATO HUWAILA, INA JIN DADIN YANDA KIKE BANI KULAWA HAKA, YARKI NA GAISHE DA KE, PAGE DIN NAN NAKI NE KI YI YANDA KIKE SO DA SHI NA AMINIYAR ARZIKI* Momy na zuwa hannun Rauda ta damka ta jata ta nufi ciki da ita wanda hakan ya sa da sauri Hafsat ta bi bayansu Tana shiga dakin Hafsat da ita ta tsayar da ita a nan, kallon tsaf da ake fadi shi Momy ta yiwa Rauda a dan kankanin lokaci kafin take juyawa ta fice a dakin Rauda sam bata gane abinda ya faru ba, bata iya gaishe da matar ba har ta fita sai da Hafsat ta kama hannunta ta zaunar da ita gefen bed dinta wanda yake gyare tamkar tana gidan , Ajiyar zuciya ta sauke kafin take cewa" wannan itace mahaifiyarmu Rauda Tamkar ta daki idannuwan Rauda irin yanda ta kwalalo su cike da tsoro Murmushi Hafsat ta yi, ta ce" ki tafi da momy tamkar yanda zaki tafi da mamanki, momy mace ce mai saukin hali ga wanda ya dauketa da mahinmanci, tana da saurin hawa sannan tana da saurin sauka, ki dauki momy da mahinmanci ki kusanta kanki da ita na tabatar maki zaki ji dadinta fiye da tunaninki Da kai Rauda ke amsawa Hafsat, har ta gama yi mata magana da sakata a hanyar da zata samu sasauci wajen mamansu, Bayan ta gama ta mike tana mai cewa " ina zuwa Ficewa Hafsat ta yi ta baya ta bula tsakar gida , nan ta tarar da Yayanta yana ta harkokinsa yana kara karban gaisuwa Gannin Hafsat ta tsaya daga nesa sosai sannan ta tsare shi da ido ya tabatar masa da tana son yin magana da shi dan haka ya samu ya sulube a hankali ya nufo wajenta Yana zuwa ba tare da ya jira ta fara magana ba ya ce" ina take? Me take? Ya momy ta karbeta? Hafsat ta yi murmushi ta ce" tana dakina yaya Daga haka bata kara komai ba ta yi gaba tana fadin bara na samo mata wani abin motsa baki Ya dan jima a tsaye kafin yake daga kafarsa ya nufi dakin hafsat Har yanzu tana zaune inda Hafsat ta barta aman ta tsurawa waje daya ido A hankali ya turo kofar ya shigo wanda hakan ya sa ta dago dan gannin ko waye Gabanta ne ya fadi ta yi saurin zamowa kasa kanta a kasa murya na dan rawa ta ce" iiiiiina kwana sire Bai amsata ba haka ya taho har kusa da ita ya duka ya kama kafadunta da kyau ya mikar da ita ya yi masu masauki gefen bed din wanda take kara yin kasa da kanta cike da tsoronsa Da kyau ya riketa a bakin bed din kafin murya can kasa ya ce" har yanzu Sire din nake? Bama wannan ba wa ya baki izinnin fitowa da hijabi mai color din da zai kara haskaka fatar ki? Da dan mamaki ta dago ta zuba masa ido, shi kuwa ya dage mata gira guda wanda hakan ya saka ta ji mugun nauyi ta sada kanta da sauri So take ta saka dan tazara a tsakaninsu aman fir ya riketa ya ki bata damar hakan Hafsat ce ta shigo da salama wanda ta ja da sauri zata juya Sudais yayi kiranta Dawowa ta yi kanta a kasa ya yi mata nuni da ta ajiye kofi mai dauke da shayi Tana ajiyewa ta juya tana dariya a kasan zuciyar tana taya yayanta adu.ar dacewa da samun soyayar abinda yake so Dauko shayin yayi, ya kai bakinsa ya surba dan jin zafin, Murmushi ya yi ya dago habar Rauda ya saka idauuwansa cikin nata, du yanda ta so karta kale shi abin ya gagara haka ta tsinci idannuwanta a cikin nasa, ji tamkar tana iyo ne a cikin idannuwansa sannan wata kwala da take gani a konce a cikin idannuwan nasa su suka saka nata sukai mata nauyi Lebensa ya motsa a hankali wanda ta yi imanin da bata tsare shi da mugun kallo haka ba da ba zata ji abinda yake fada ba A hankali ya ce" Ha bakinki ki sha shayin nan kar ki bar mana cikinmu da yinwa Bata iya musa masa ko yinkurin kuma kwace kanta ba, saima ji ta yi bakinta ya buda ya karbi shayin da ya miko mata sai dai ji ta yi ya mata zafi Da sauri ta dawo a hayacinta ta shiga hura lebenta da har ya danyi ja na wahala Da sauri ya dago habarta ya matse mata waje sosai , da bakinsa yake hura mata leben nata wanda har ya fita nuna damuwa Shi kansa bai san ta ina ba, bai yi masa shawara ba sai gani yayi harshensa ya bi umarnin zuciyarsa , wato ya ciro jarshensa ya kai kan leben Rauda cikin nutsuwa ya shiga lashe wajen da ya kone Idannuwa ta zaro, ta yi wata irin dan ja da baya wanda ya farkar da shi Shi da kansa sai da ya ji dan nauyi kadan wanda bai taba ji dan kawai ya dan yi irin haka ba A hankali ya dan raba jikinsa da nata ya tatara mata hijabinta ya kontar da ita saman bed din, Kafafuwanta ya dago ya dora mata su comfortable Dan dukawa yayi sosai kusa da kanta yana dan shafa gaban goshinta wanda hijabin ya dan zame, sabon salon rage muryar da ya samu ne ya yi anfani da ita wajen cewa" ni fa ake tatali ba ni ke tatalin mata ba wife, Ki huta Yana gama fada ya mike ya fice ya bar Rauda da gajiya tamkar ta yi aiki, da mugun kasala da wani irin yannayi A nan Rauda ta tare, sallah kawai ke tashinta tana yi ta dawo ta afka duniyar tunani har dare yayi sosai Asuba allhairi amaryar Sudais Washe gari, da asusuba Rauda ta shirya ta saka doguwar abayarta ta.nemi Hafsat da ta kaita wajen momy Rakata Hafsat ta yi ta shiga da salama Momy dake zaune tana adu.a ta shafa ta dago tana amsa su Har kasa Rauda ta duka kanta a kasa ta ce" barka da asuba momy Momy ta amsata ba laifi Rauda mikewa ta yi gabanta na dan faduwa gannin momy zata ninke salaya ta karasa ta dan duka ta karba ta ninke ta ajiye ta dan duka ta ce" a fito lafiya momy Da ido momy ta rakata, ajiyar zuciya ta sauke ta shiga shiryawa Mama yaune Adu.ar arba.in din matarsa, na tabata zan same shi a can kin ga sai na jefi tsuntsu biyu da dutse guda na ga matar da aka ce yar gidan sarauta ce ya auro sannan na ganshi na kuma shigar da kaina, sarah kawai nake jira ta zo mu fice gashi har karfe goma ta yi bata zo ba Kai kawai mama ta girgiza ta ci gaba da tsince shinkafarta ta hausa bata iya cewa Aisha kanzil ba Tana nan zaune sai ga hon din Sarah , da sauri Aisha ta tashi ta dauko gyalenta ta yafa tana fadin sai na dawo mama Murya a sanyaye Mama ta amsata da Allah ya tsare Tafe suke suna hirarsu ta yanda zata tunkari Elhaj Sudais , sannan su ga amaryarsa dan su san da wa zasu yi kishi Daga kofa suka ajiye motarsu domin du an hana shiga da mota kowama idan ya zo ajiyewa yake a kofa Cike da rangwada suke takawa suna kutsawa wanda direct Aisha ta yiwa Sarah jagora bangaren Momy domin wancen zuwan da suka yi sun hadace wajen Zaune su Rauda suke tare da Hafsat da kawayen hafsat daidai lokacin da su Aisha suka shigo cikin falon da yar salamarsu Irin yanda gaban Rauda ya yanke ya fadi bata san lokacin da ta mike tsaye ba ta dago yatsarta tamkar ta ga wanda ya mutu ya dawo ta...... Page na gaba na tare da cakwakiya, surprise , abin tausayi, bugawar zuciyoyi aman zai zo ne idan kun karfafa comment dinku🙂 *❣IDAN KA RAINA INDA KAKE❣* Na: *SAJIDA* *_LITATAFAN MARUBUCIYAR_* *_Duk Karyar kada_* *_Yar Mahaukaciya_* *_Neman na kaina_* *_Bani da zabi_* *_Daga tafiya daukar soja_* *_Idan ka raina inda make_* *🌈KAINUWA WRITERS✍🏼 ASSOCIATION*🤝🏻 ```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}``` https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation 4⃣0⃣ *DAN ALLAH A JI KUNYATA KAMAR YANDA NAKE JI, KAWAR DA KAI DA MAYAR DA KAI TAMKAR SAKARAI WANDA BAI SAN YARE BA DAN A ZAUNA LAFIYA NE, THX* Irin yanda gaban rauda ya yanke ya fadi , bata san lokacin da ta mike tsaye ba ta dago hannunta da yatsarta manuniya tamkar ta ga mamacin da ya dawo, tana kokarin yin magana Humaira da tun zamanta idonta a kanta ta dan juya dan gannin menene? Domin wajen du suna dan kakayatunsu kun dai san taron mata Bakinta na rawa muryarta can ciki take fadin" auauaunty aunty aunty Hafsat ta juyo ta ga Rauda a wannan yannayin daidai lokacin da suma suka ganta su Aishar Cike da mamaki suka nufo da niyar zuwa wajenta Da sauri Hafsat ta mike ta kama hannunta suka zagaya ta dayan bangaren suka fice a falon hakan da suka yi ya sa su aisha suka bi bayansu Wajen lambu Hafsat ta nufa da Rauda wanda yake bangaren Sudais na da, wajen da yakan je domin hutu, ko yayi tunani mai zurfi wajen a daidai lokacin suna tsaye da Samir yana bashi wasu takardun da zai je ya kai sanadiyar kiran gagawa da akai masa kuma yana jin nauyin datijom domin takardun wasu filaye ne manya manya da ya daga dan inda suke ba waje ne mai kyau ba gwomnati ta shiga Sauri sauri Hafsat ke jan rauda da karfi domin du jikinta ya saka ta wani firgice har nadin dan kwalin da ta yi ya konce rabi saman kanta rabi yana reto a jikinta Suna shiga Hafsat ta kaleta da niyar yin magana muryar AISHA ta katse su, Aisha ta shigo Sarah na biye a bayanta suma cikin dan hanzari domin wannan ai kanwar Elhaj Sudais ce, ko me ya hadata da Rauda har take taba hannunta haka? Ko dai wani mai aikin su Hafsat ne ya auri Rauda? Aisha na shigowa ba tare da ta tambayi yar uwarta yaushe rabo ba, lafiyarta da sauransu kawai sai ta bura ta ce" Rauda, me kike a gidan nan ne? Ko dai mijinki a nan gidan yake aiki? Gaba daya jikin Rauda ya kwashi rawa gannin ga auntynta ga Sarah , da wuya ta iya fitar da kanta, abinka da wanda ya tsorata da sauri ta matso ta kamo hannun Aisha , murya na rawa da alamar kuka ta ce" walahi Aba ne ya hada Aunty, walahi bana sonsa kamar yanda ya tsane ni, Aunty ki fahimce ni karki yi min muguwar fasara dan Allah, ke dai kin san ko ni wacece, ke zaki iya fadi abinda zan iya da wanda ba zan iya ba, kuma kece shaidar nima ban san da auren ba sai da Aba ya fada mana a tare Du wannan sambatun maganar da Rauda ke yi Aisha ta tsareta da kallo ne na tausayi, a gaskiya tana tausayawa kanwarta kennan har yanzu basu shirya da mijin nata ba? Shi yasa da ta ganta ta rikice, gaskiya aba ya iya hukunci, han ai Allah ya taimake shi ba ita yayiwa haka ba da ya sha kunya Aisha ta taba kafadar Rauda ta ce" haba lallana, menene? Har yanzu baki shirya da mijin naki ba? Rauda gannin Aisha bata fahimci inda ta nufa ba ya sa ta shiga gurgiza kai tamkar ta yi laifi mamanta ta tsareta da bulala, murya a sanyaye ta ce" shi ne fa aunty? Aisha ta ce" mene? Wai meye ne? Gannin Rauda ta kasa amsata ta juya wajen sarah dake kallon Rauda da yannayin tambaya, irin shigar jikin Rauda da yannayin fatarta bata nuna a cikin wahala take ba duda ta dan fada aman ba wani can ba, aman wa take aure haka? Ki waye shima ba laifi somin gaskiya sam Rauda bata yi kalar wace ke cikin wahala ba Kafin Aisha ta yi magana Sarah ta matso tana mai cire gilas din idonta ta ce" kinga Aisha mu yi mu je mu gama abinda ya kawo mu tun kafin yama yayi, domin na ga kanwar nan taki banda jaje ba abinda ta iya Aisha ta sauke ajiyar zuciya ta kuma kallon Rauda ta ga du a rikice take tamkar ta yi karya, sai zufa ke tsatsafowa daga goshinta, hankalinta ta bata da kyau domin ta sani haka kawai Rauda bata irin haka sai da kwakwaran dalili, muryarta ta kausasa ta ce" menene? Kukan me kike? Rauda ta kara riko hannun Aisha sa kyau ta ce" ni kaina sai da ya zo na ganshi!!!! Ta karashe tana mai fashewa da kuka Aisha cikin kufula ta ce" wai wa? Rauda ta dago da sauri muryarta na rawa ta ce" shishishii......elhajin, Elhaj Sudais din ,..........shi Uban masu gidan Gaban Aisha ne ke faduwa haka kawai tun kafin ta idasa fahimtar inda ta nufa, ta ce" Elhaj Sudais, wani abin yayi maku ne? Mijinki aiki yake yi masa ko? Wulakantaku yake ko me? Rauda ta jimke hannun Aisha , cike da sakin baki ta ce" shine Aba ya aura min, Aunty shine mijina! Aman aunty mu dukanmu a rashin sani aka yi, baya sona nima bana sonsa, aunty daman cewa na yi daga an yi adu.ar arba.in din matarsa zan nemi sakina na nemi alfarmar ya aureki, Aunty ni kaina ban san haka zata faru ba sai da na ganshi Sudais dake tsaye shi da Samir mutuwar tsaye yayi, ba abinda ke dukan kunnensa sai bana sonsa baya so na, soma nake ya sakeni! Karar mari ne ya saka shi kallo wajen da sauri Aisha da ta yi mutuwar tsaye ce ta daga hannunta ta wankawa rauda wani kafirin mari mai kausashen kara da zazafen zafi, kafin ta sauke hannunta na dama ta kuma wanka mata da na hagu a dayan gefen, ta cakumi wuyan rigarta wanda har rigar ta dage, sosai ta yi mata shaka wanda Rauda taki kokarin kwatar kanta ta tsaya tamkar wata sauna Aisha na jijigata Da gudu Hafsat ta zo ta shiga kiciniyar kwatar Rauda , Wanda Aisha ta yi kukan kura ta hankadasu gaba dayansu Rauda da kwatakwata ba laka a jikinta ta je zube nan Hafsat kuwa ta yi tagataga zata zube da kyar ta rike kanta Zaman yan bori Aisha ta yi tana kallon Rauda, ta jima kafin take kwala wani uban ihu ta ce" mijinki? Mijinki ko mijina? Mijina ne dan ubanki! Nace mijina ne Rauda Ahmad! Ni da ke wa ya fara ganninsa? Ni da ke wa ya ce yana sonsa? Na gina mafarkin rayuwana ne da shi, ko bashi da komai na tsara rayuwana ne da shi, me ya kaiki gangancin nan? Kece shaidar irin azabar da na tabatarwa du macen da ta yi gigin rabarsa! Aman shine ke kika aure shi? Tana gama fadar hakanan ta mike ta nuno Rauda da yatsarta da irin kallon nan mai shige da kashedi ta yi kak da bakinta ta juya ta bar Sarah nan tsaye tamkar gunki, Sarah abin tsoroma ya bata, wai daman Rauda ce Elhaj Sudais Uban masu gida ya aura? To ta yaya aka yi haka? Daman aban ya san ko waye? Ina ba zai yiwu ba dole sai ko ya kara da ni ko ya saketa kowa yayi biyu babu dan ba zai yiwu yar gidan Ahmad mai faskare ta auri wannan mutumin ba, ya fi karfinta Itama da sauri ta juya ta bi bayan Aisha wace ta nema ta rasa Idan ka ga Aisha na sheka gudu zaka rantse da mahaukaciya ce, fuskarta shabe shabe da hawaye, idannuwanta jajir, majina wata kan wata Gudu kawai take ita kanta bata san iya gudun da ta yi da kafarta ba, iya adadin lokacin da ta dauka tana yi ba, sannan kltn da ta ci ba, ita dai ta ganta a anguwarsu harma mutane na binta da kallo wasu su mike suna masu tambayarta lafiya? Wasu su shiga hangen bayanta ko biyota aka yi? Wasu kuwa su zundo bakinsu a fili su furta" kontan gidan Malan Ahmad ce, tana yawon nan ita batai auren ba ita bata zauna a gidansu waje daya ba, mai yiwuwa ta jajibowa kanta hauka ( wa iyazubillah ) A dubu ta afka gidansu, Tana shiga ta nufi malan dake kokarin ajiye faskarensa ta tsaya tana kallonsa tana muguwar shashekar kuka, Hannayenta ta cusa cikin kanta ta yamutsa, murya a shake dan irin kukan da ta ci ta ce" na kasa yarda da abinda ya faru Aba, Aba wa yake auren Rauda ne? Mama da ta fito da ruwa a buta ta saki butar ta fadi kasa, tsoro ya hanata karasowa dan a yanda ta ga Aisha bata so kalma daya ta fito a bakinta kan Rauda dan tana tsoron ta furta Rauda ta mutu Malan Ahmad kansa gabansa sai da ya fadi, me ya sami Raudarsa? Rabonsa da ita tunda ya kaita bai kuma bi ta kanta ba, meke faruwa ne? Aba ya ce" Aisha Lafiya? Aisha ta daki garun dakinta da hannunta na hagu cikin karaji ta ce" Aba wa yake auren Rauda nake son ji! Malan Ahmad ya matso da sauri kusa da ita ya ce" wani abin ya faru da raudar? Shi nake son ji Aisha ki daina fadar min da gaba dan Allah Aisha ta juyo wajen Mama, da sauri ta karasa wajenta ta riko hannunta suka matso kusa da Malan ta ce" kin san wa Rauda ke aure? Kin kuwa san wa take aure? Rauda na auren burin raina! ABA, wanda kika ce shine mahaifina , ya yi zabunta ya aurawa Rauda mutumen da nake son aire, Mama Rauda na Auren Elhaj Sudais mama Da sauri Mama ta dafe kirjinta, nan take ta shiga maimaita innalilahi wa inna ilaihi raj.une, Kallonta ta maida wajen malan tana jiran jin karin bayani Malan yayi sokoko shi kansa yana jin wani aabon magana kuma, shi dai yakan tsinci magana Aisha na yawaita fadin Elhajinta, Elhaj sudais dinta, aman daman Elhaj Sudais din da Ya aurawa Rauda? Tabas shi ne ( Aba ya san wanda ya aurawa Rauda, domin mahaifin elhaj sudais ya fada masa komai a tsanake bayan daurin auren sannan ya fada masa suna son a kaita wannan gidan, bai fada masa dalili ba shi kuwa bai yi tambaye tambaye ba, shi dai ya san Elhaj sudais ya fi karfin ya saka matarsa a muhalin nan, sai kawai ya taya shi yin abinda yake muradi ya ringa baiwa Rauda sakon Sudais idan direba ya kawo ko Samir, kuma ya karbi na wajen Rauda ya basu ) har ga Allah, Har cikin zuciyarsa ya ji wani iri, sannan ya ji tausayin Aisha, koda soyayar Da take yiwa Sudais ba wai ta ko yana halin rashi zata iya zama da shi ba domin idan bashi da shi ya tabata Aisha ba zata iya zama da shi ba, aman duda haka ya sani so ciwo ne Dan sanyaya muryarsa yayi ya ce" Aisha, ki yi hakuri, Du abinda kika ga Allah ya dorawa bawansa dan ya jaraba imaninsa ne, idan kin yi hakuri na tabata zaki girbi alkhairin hakurin, Aisha da muryarta ya gama shakewa cikin yannayin taratsi ta ce" bana so, bana so, ka yi shiru, a yau ina da kokonta idan har kai ka haifeni Mama da sauri ta ce" Aisha! Aisha ta juyo wajen mama ta ce" mama ina kokonton hakan, mama na fada ! Na fada! Mama ta daga hannu ta wanka mata mari abinda bata taba yi mata ba, sannan murya na rawa ta nunata da yatsa ta ce" mace bata taba yin shege ba, ko cikin dubu ta san waye uban yayanta! Ban taba kauce hanya ba, ina adu.ar da na kauce gwara Allah ya karbi raina, ki tauna harshenki kafin ki jefemu da magangannu mararsa fa.ida Aisha dafe da kuncinta ta tsare su da kallo, magaifinta jikinsa a mace yana ta kukan zucin yarsa bata da tarbiya , sai mama dake kuka tana tsaye itama tana kallon Aishar Juyawa ta yi ta harhada kayanta cikin yar jakarta gari yayi zahi ta fito da hijabinta buguzun buguzun zata fita Ido mama ta zaro ta nufota ta kamata ta ce" Aisha ina zaki je? Menene haka wai? Me yasa kika fiye daukan duniya da zafi? Aisha ta ce" tafiya zan yi inda na fi wayo mama, na bar maki gidan! Kokarin rikera mama take tana daukaka kukanta Aisha ta fizge ta fice Da sauri ta juyo ta zo wajen malan tana nuna masa da ya hana Aisha fita, Hannayensa ya saka ya jawota jikinsa ya rungumeta da kyau yana dan bubuga bayanta (😳), murya irin ta manya ya ce" zata dawo, in sha Allah kuma zata dawo yanda ta fita domin sai ta fita zata daina *RAINA INDA TA KE* mu sakata a adu.a kar duniya ta yi mata mugun horo Jikinsa a mace ya karaso inda take yashe, A dan tsorace take kokarin tashi ya mika hannu ya tayar da ita tsaye Kunace mata waje yayi, murya can ciki ya ce" *YA AKA YI KIKE MIN IRIN WANNAN KIYAYAR HAKA?* Fuskarta da take kawarwa tana ta sheshekar kuka, abin yayi mata yawa, ya rike da kyau ya saka idonsa cikin nata ya ce" *sai dai ki sasauta kiyayarki domin rayuwa da kiyaya ba kyau fa, kuma kinga aurena ba saki* Yana gama fada ya saketa cike da jin ciwon magangannunta wai bata sonsa ! Shi a ina ya taba ce mata baya sonta? A gaban Hafsat, da Samir, harda bakin fuska ta furta kalaman nan *❣IDAN KA RAINA INDA KAKE❣* Na: *SAJIDA* *_LITATAFAN MARUBUCIYAR_* *_Duk Karyar kada_* *_Yar Mahaukaciya_* *_Neman na kaina_* *_Bani da zabi_* *_Daga tafiya daukar soja_* *_Idan ka raina inda make_* *🌈KAINUWA WRITERS✍🏼 ASSOCIATION*🤝🏻 ```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}``` https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation 4⃣1⃣ Yana komawa ya zauna cikin mutane yayi jigum da shi, su Abansa ne da jama.arsa datijai da samari, *Bana son sa* ya daki zuciyarsa wanda ya ji tamkar ta watsa masa mari, bana son sa, ya sakeni, Kawar da kansa yayi ya ce" *MATA, NI INA SONKI* Wayarsa ya lalubo ya sami number Hafsat, Tana dagawa bai tsaya dogon turanci ba ya ce" ku fito direba ya kaiku gida, Hafsat na kokarin yin magana ya katse kiran Dubanta ta mayar wajen Rauda dake zaune tana jan carbi hannunta na dama na hagun kuwa ta talabe fuskarta Momy ce ta shigo da salamarta ba mai kara ba, tana zuwa Rauda ta gyara zamanta irin dai zaman gaban sirikai ga mai kunya 🤣 Wajen madubin dakin Hafsat Momy ta zarce ta jawo ta bude ta ciro wata leda da ta yi ajiya ta taso da niyar tafiya Hafsat ta ce" mom yaya ya ce mu juya gidansa yanzu Jim ta yi ta juyo, ta kali Hafsar kafin take maida dubanta wajen Rauda da take ji tamkar tace ba zata je ba, sai ji ta yi momy na cewa" ALLAH YA TSARE Haka suka fito wanda bayan sun fito suka ga fitar motar Humaira, da alama dai ba su kadai aka kora gida ba Direba na kaisu gida Hafsat ta fice ta shige, da gangan take yiwa Rauda fuska, taki ta kulata ko yayama A hankali jiki a mace Rauda ta fice ta bi bayanta sai dai wani tashin hankalin Su Humaira ne da kawayenta biyu gogagun yan bariki an baje koli ana rangada buda ana ta dariya irin dariyarnan mai kara tamkar an yi masu albishir din ba zasu mutu ba aljannah kawai za.a saka su! Cikin sanda da takun da bata so a lura da ita take kokarin shigewa bata san ta makaro ba domin kawar Humaira wace ta zo karbar gold dinta ta kai ta anso kudin ta ganta Iye? Haka ake maki bariki a cikin gida kawas? Wannan kugu haka? Kike yarda ana saka abaya kawai a cikin falo????? Humaita ta juyo, gannin Rauda ta buga wani uban tsaki, ta ce" daga baya ba, mijina ya fi karfin yan yawo a titi suna neman cin yau da muhalin kontar da kai kafin gari ya waye a fantsama, ke uwarsu fa har gobe yawon maula take! Kuma du isar yarinya da wani fi.ilinta a banza domin mijina bai damu da shinfidarta ba Wani irin birki Rauda ta ja ta tsaya, juyowa ta yi ta sauke kwayar idannuwanta da sukai mata jajajir sakamakon kukan da ta sha, a kasan zuciyarta take ayanna wai wannan matar me take nufi da ni? Sanyin halina? Ba yana nufin ina daukan iskanci kan iyayena ba? Su kuwa meye laifin su? miji? Gaba daya kanka ne nake gannin wannan abubuwan? ELHAJ SUDAIS kai ka yi min, matarka ta yi min, duniya ta yi min, gidanmu a yi min? Kanka kai daya kwalin kwal? Na sani kai din nama ne daya cikin miya, ka zamto lu.u lu.un al.umah ! Ido Aunty ta rufe ta wanka min mari sanadiyarka! Ta yi ikirarin ni da ita mun shiga takun saka....... ga matarka na zagar min iyaye Ke ubanta fa almajiri ne, kuma faskare yake na itace kofa kofa kafin ya samu naira dari sai ya wuni yana bin rana Hafsat ce ta fito da sauri ta nufo wajensu domin magangannun da suke tun karfi suke yi dan su hasalata, har hafsat dake danne zuciyarta ta kasa ta fito ta ce masu su daina ba kyau, da sauri ta karaso wajensuta ce" haba Aunty, haba aunty, menene wannan din dan Allah? *HAFSATTTTTTTTTTTTTTTTTTTTTTTTTTTTTTTTTTTTTTTTTTTTTTTTTT* .....da mugun karfi ta ji sunnanta kamar daga sama Waigawa suka yi a tare wajen da amon muryar ya fito sai ganninta sukai ta tunkaro wajensu a mugun harzuke Tana zuwa ba tare da wata wata ba Rauda ta daga hannunta ta tsinke Humaira da wani gigitacen marin da ya saka Humaira gannin walkiya , Kan uba , kawayen Humaira suka furta tamkar an hada bakinsu sannan suka dora hannu a saman kai, Abinka da mai bltng tuni fuskar Humaira ta haye san hannun tas ya fito saman fuskarta, kawayenta tsofafin guzumaye suka zazaro ido, mai suna Laure ta.ce" kutumar ubancen, ke Humaira lale wannan karon an dauko maki ruwa dafa kanki, wannan mari haka ? Aman gaskiya idan har kika kyaleta ta gama shawo da ke Humaira abin ya zo mata a ba zata, me? Mari? Ita anya ko tana yarinya an taba marinta kuwa? Kuma mijinta ba mai duka bane, shi ya san wajen dukanta, aman yau gashi yarinya karama ta daga hannunta ta sharara mata mari, rasa mai zata ce ta yi sai ta ce" ni kika mara? Rauda dake tsaye kuda da Hafsat , Hafsat sai zaro idon mamaki take tana kara kallon Rauda, daman ta iya fada? RAUDA ta ce cikin dakakiyar murya" an mare kin, ko kin fi haka tsufa kika zagar min iyaye sai na nuna maki na san darajarsu, kuma a kan menene kike wannan abin? Kan Miji? *MIJIN MU?* bani da niyar zama da shi a da, aman walahi zaki gane ba a hayagaga take ba, zaki banbance aya da tsakuwa! Du wace bata bi ni a laluma ba , zamu kure iskanci ni da ita daga ke har du wata mai jin tashen iskanci dan na Auri ELHAJ SUDAIS! *yanzu na dauri damarar zama da shi shege ka fasa* Humaira wani irin duhu duhu take ganni, kukan kura ta yi ta shigi Rauda da dukan karfinta da duka inda kawayenta ke turata Da dukan karfinta take tarewa inda Hafsat ta samu ta banbareta daga jikin Humaira ta jata kiiiiiiiiii da gudu sukai dakin Hafsat din domin shine a kusa da wajen Sai bayan sun shiga Rauda ta ga gashi a hannunta da sauri ta yar , Hafsat ta bi abin da kallo karin gashin ne Rauda ta tsigo daga kan Humaira ita kuwa ta cira mata mabalan riga sannan ta yage mata wuya da hanu Hafsat ido kawai take zarowa tana kallon Rauda, daman ta iya fada haka? Daman ta iya maida martani haka? Kennan kamar da ake cewa mutun na mayar da kansa wawa dan a zauna lafiya hakane? Bata taba tunanin akoy abinda zai sa Rauda ta daga muryarta , ta rama kai har ta kai da jikinta ya tabu ba, ya ilahi Raudar ce kuwa? Kai yau ta birgeta karshe, lalai in dai haka ne hankalinta ya konta ta yarda Rauda ta san me take yi, ta tabata irin wulakancin da yayarta ta yi mata ya sa zuciyarta ta fara kekashewa, idan kuwa hakane ai abin yayi dadi ta kaita bango ya kasance ita dinma ta daina raga mata domin na ga yayar nan tata sam ba tausayi da tunanin abinda ya dace a lamuranta ( to fa😌, an kai Rauda bango ta fara duka🙆🏽) Aisha bata zame ko.ina ba sai gidan su Sarah, Tana zuwa da kuka ta zube jikin aunty ta kwashe komai tana hawaye ta fada mata Da kallo aunty take binta, ta karewa jakarta kallo, dankari yau ake balaki, tana nufin a nan zata zauna? To a inana zara ajiyeta? Ita kadai sai yarta suka san sirin gidan nan..... aman bara Sarah ta zo su yi shawara ita baban abinda ma zai sa ta rike Aishar dan su kwace Uban masu gida itama ta samu fada a wajen mijinta domin Sudais din uban gidansa ne Aunty ta sauke ajiyar zuciya ta ce" aman ya aka yi shima ya fi son Raudar a kanki ne? Gaskiya bai yi mana adalci ba Aisha tana kara sheshekar kuka ta ce" haka muka taso, shi kulun ni yake sakawa a gaba yanai min fada ita kuwa sai dai ki ji yana fadin Allah ya yi mata albarka, yanzu mai gaba daya ya bata mutumin da nake so Auntu ta yatsina fuska a ranta ta ayanna kike aon kudinsa dai, a fili ta ce" ina ai kema ba zaki yarda ba, ba kince ta ce ba abinda ya shiga tsakaninsu ba? Ai dabara zaki mata ya kasance ta takura shi ya saketa ya aure ki ko? Aisha da idannuwanta suka rufe sai kawai ta ga hakanma za.a yi, aunty ta kawo kyakyawar shawara Aunty gannin kamar ta yarda da shawar nata ya sa ta ce" tashi ladi ta kaiki dakin Sarah Mikewa Aisha ta yi ladin dake rabe ta mike da sauri har kamar ta fadi ta raka Aisha cikin wani dan koridor ta nuna mata dakin Aisha cikin dan gadara itama yar gida ta ce" ki kai min kayan ciki mana Da sauri ladi ta kali Aisha kafin take sada kanta ta ce" ki yi hakuri hajia, Uwar gidanmu ta hane mu rabar dakinta sai in gyara za.ai mata shima idan tana nan ki yi hakuri Tana gama fadar haka ta juya da sauri ta bar wajen Tura dakin ta yi ta ja ta tsaya, Gaskiya Sarah babar yarinya ce, domin ko mamanta bata saya mata ba zata nemo kudinta ne ta sayi abinda zai gyarata, bed daya ne a daki sai irin sif din nan na roba mai hotunan barbi cikinsu ne wani kayanta wani takalmanta, sai wajen madubinta dake cike da kayan shafe shafe da su turare dai da sauransu Kayanta ta raba nan kafin take zuwa ta dare saman gadon Sarah , abinka da ba sabon ba sannan ana kwadayin hakan nan da nan baci ya kwasheta............ Yar mutan niger ce 💓💓💓💓💓💓💓💓💓💓💓💓💓💓💓💓💓💓💓💓💓💓💓💓💓💓💓💓💓💓💓💓💓💓💓💓💓💓💓💓💓💓 *❣IDAN KA RAINA INDA KAKE❣* Na: *SAJIDA* *_LITATAFAN MARUBUCIYAR_* *_Duk Karyar kada_* *_Yar Mahaukaciya_* *_Neman na kaina_* *_Bani da zabi_* *_Daga tafiya daukar soja_* *_Idan ka raina inda make_* *🌈KAINUWA WRITERS✍🏼 ASSOCIATION*🤝🏻 ```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}``` https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation 4⃣2⃣ *ALLAH KA KASHE MU DA IMANINMU,* Sarah na zuwa ta shige dakin mamanta dan shafa mata wannan labarin mamanta ta dakatar da ita ta shaida mata ta ji komai sannan ta fada mata Aishar ma na nan ta baro gidansu tana dakinta Bata fuska Sarah ta yi ta ce" haba mom haba mom, wani irin dakina kuma? Ke ki kawota naki mana? Haka kawai dan ta takura min? Aunty ta ce" ke baki da hankali? Baki san sai da na gwalgwali du wani shege mai bakin tsiya kan kar ya yarda elhaj ya ji tana gidannan ya hada daga ni har ita ya wulakanta mu a gaban idon kishiyoyi ba? Idan na barta a dakina kin san sarai du safiya sai ya bi dakunanmu ya ga me muke muna bama dai kwanan masa da ac da sauransu kema san ban san ya akayi kuke dasawa ba har dakinki ya fi karfin shigarsa ba aman da ai sai dai nima na koreta , dan haka hakuri zaki yi na dan kankanin lokaci idan muka gama abinda muke so da ita sai mu koreta! Sarah dai ranta bai so ba ta mike buguzun buguzun ta fice ta nufi dakinta Tana zuwa da gadara ta bude dakin ta shiga, sai dai hango Aisha ta yi dadaya saman gadonta ya sakata yi mata kallon tsaf Wani sakaran murmushi ta saki, a kasan zuciyarta ta ayanna nama har gida..... 🤦‍♀ Tun karfe shida da wani abu take jin magana sama sama , firgigit ta farka ta fara raba ido ta yi zaune saman bed din ta kai dubanta wajen da Sarah take sai ta ganta konce ba riga a jikinta sannan hannunta na wani sasa na jikinta Da sauri Aisha ta kawar da kanta tana mamakin meye kuma wannan? Sai dai bata gama ba kanta amsa ba ta jiyo muryar aunty tana fadin" ELHAJ walahi walahi rabin kofi ne na kara awon jiya sakamakon rashin koshi da ake, kuma naman nan na kan table ban taba shi ba, kamar yanda ka hana kace a ringa dorawa saboda banda kama dan mutane kulun ana dorawar kuma bama ci, kudinka kuwa ai na biyaka na fada maka manufar kyautar nan da na yi da su, ka yi hakuri dan Allah kar ka sake ni Muryar wani baban mutun ta ji ya ce" ki rufe min baki, ke kam an yi asara a kayanki, ke ke nemo min shinkafar ne? Baki da godiya, sannan kin ga yarana suna yi min korafin mota na baki mota ban baiwa sauran ba, ni nakan manta lokacin da kike shigata haka , haka kika tarda budurwata kika ci mata uwa, to ki kiyayi ranar da zan saka ki a hannuna! Kar ki kara min awo gidana ne ni ke nemana dan haka a daina yi min shishigi Yana gama fada ya fice ta zauna ita kuwa ta yi zaman dirshan A hankali Aisha ta shiga kikifta ido, idan dai ta fahimta mahaifin su Saeah ne ya gama wannan wulakancin? Me hakan ke nufi? Du wannan uban dukiyar? Aman ai ba za.a kirashi talaka ba domin ko a balbalin gidansa zaka gane ya nema ya samu !mahaifin Sarah irin mutanen nan ne masu da shi, mai kudi ne sosai sai dai kudinsa bai andani iyalansa ba, komai na gidansa a ka.ide yake, ya kasance mutun mai mugun son kansa, yakan dauki mace ya fita da ita kasar waje tunbama Maman su Sarah ba domin ga fari ga kyau sai dai inda kuka saka kafa da shi kun raba hanya, sai bukatar a ganku ya taso zaki ganshi, mahaifiyar Sarah tana kasuwanci sosai hakan ya sa ta fi karfin wasu abubuwan harma take kona ran kishiyoyi wajen nuna masu cewar shi yake bata , tana saka abinda take so ne ta ci dadinta da yarta sai dai idan ya tardota daki ita da jaka du daya, gashi da shegen bin mata yana raba masu kudi yana kara su iyalansa kuwa ya ka.ide masu komai, dan mugunta ya tsara masu abubuwa wanda idan wani ne ya shigo daga waje zai yi tsamanin wannan gida gidan daula ne daman ya samu shigewa ya wanke goma ya tsoma biyar ya side biyar, sai dai da ka shiga zaka jika tamkar a kaso kake, matan basu da damar kawo yan uwansu su zauna kirikiri zai fito ne ya nuna bai yarda ba kar a dora masa nauyi Bata gana mamakin abinda ta saurara ba ta shiga kokarin sauka a gadon dan zuwa ta dauro alwalah sai dai me sutura ne idannuwanta suka ci karo da su, wato irin maganin nan na tsarin iyali wanda gogagun yan bariki da kuma matan aure masu bukatar yin tsarin iyali ke andani da shi ne nan yashe wanda Sarah ta bala ta sha kafin ta konta dan a kulun take sha dan gudun bacewar rana, itama Aisha ta sanshi ne sanadiyar wata kawa da ta yi matar aure wani lokaci zata sha take tambayarta bata jin dadi ne ? Nan ta bude baki shaaaaaaa ta shatata mata komai domin itama matar ba dai kamun kai ba Da tsoro tsoro ta dadawa Sarah duka tana fadin ke Sarah ke sarah tashi Da sauri Sarah ta mike tana sosa inda Aisha ta daketa tana kallon Aisha ta ce" ke meye haka zaki yi min wannan dukan?? Aisha dake tsorace ta nuna mata abin hannunta ta ce" me me kike da wannan ke kuwa? Ko wani ya baki ajiya ne? Sarah ta hade girar sama da ta kasa ta ce" nawa ne, wani abin ne? Aisha ta ce" pil Sutura ne fa? Me ya hada ki da shan maganin tsarin iyali? Sarah ta zabga mata harara ta ce" ke malama, zan yi maki kashedi biyu, ba.a tashina a baci ko uban waye baya gigin tashina idan lokacin tashina bai yi ba, sannan ko me kika ga ina yi ba abinda ya dameki rayuwana ne ke in banda rainin hankali ke ya aka yi kika san ko na menene? To ki fita harkata idan kuwa ba haka ba zan ci maki uwa! Gaba daya idannuwanta Aisha ta zaro, ta saki maganin nan kasa tana kallon Sarah, daman sarah yar iska ce har haka? Me yayi zafi daga na tambayeki harda zagi? Ba komai zan yi hakurin har na samu abinda nake so na bara maku tsohon gidanku ke nan har gida nema gareku? Zaki ga daula gidan mijina sai na ci uwarki idan kika yi gigin rabarsa Tana gama wannan tunanin ta shige bayin Kusan a nan suka wuni har dare, Hafsat na dan lekowa sai can bayan magarib kawayenta suka tafi bayan sun dorata sosai ta hau kuwa ta yi alkawarin sai ta fida Rauda daga hayacinta kafin ta koreta daga gidanta Murmushin mugunta ta yi kafin ta daga kafarta ta nufi dakinta Rauda ta kali Hafsat ta ce" dan Allah sister ki barni na je dakina mana Hafsat da itafa a dan tsorace take an yi casun nan a gabanta ta ce" kin ga Rauda aa, kar a je ki fita su yi maki taraya kin ga su uku ne mu biyu kuma sun fimu girma kinga shekaru da kuma girman jikin kansa kinga kar aje su ilata mu Yar dariya Rauda ta yi tana nuna Hafsat ta ce" lah kike cewa na cika tsoro, Hafsat ma dariyar ta yi tace" na janye wancen maganar , gaskiya kin ban tsoro da mamaki yau, ke nifa bana bugawa aman na iya kuri wayo idan na buda bakina sai ki ji tsorona aman da naga za.a taban lafiyar jikina sai na buya Sosai itama Rauda take dariyar ta ce" kin san Allah ban san na kai haka kekashewa ba, ni daman na fiya hakuri ko a makaranta sai an kaini makura kuma fa idan na yi bugu wly sai na jiwa mutun ciwo tamkar wata kato, aman ai yanzu kuma an ajiye fannin taba lafiyar jiki, zamu goga ne ta inda ya dace an daina kishin hauka Ido Hafsat ta zaro cike da murna ta ce" kina nufin zaki zauna da yayana har zaki yi zaman kishi da matarsa? Kina nufin kina sonsa yanzu Rauda ta tsare Hafsat da ido, sai yanzu take gannin wautarta, a gabanta fa take furta bata son dan uwanta jigon rayuwarsu, ya salam aman na jima ina tafka shirme haka? Ina tunanina ya je ne?, irin murmushin sangarta ta yi ta dan daki gefen kafadar Hafsat bata bata amsar tambayar nan nata ba ta mike tana fadin " oya freind zo ki rakani na je na canza kayan nan da safema da su ya ganni kar kuma na fita matarsa ta jijiga ni .... Tambayoyi= shin Rauda ta kudiri aniyar zama da sudais dan ta fara sonsa ko dan takaicin irin wulakancin da take ganni wajen mutane daban daban da suka sako rayuwarta a gaba? Tofa tana so ta nunawa kishiya ta karbi miji shin hakan zai haifa mata da da ido kuwa? Zata bile a basajar soyaya ko zata jita a kame tamkar an kama bera? Wa zai ci wasan nan ne tsakanin Rauda, Humaira, Aisha da kuma Sarah????????????? *tsakanin Rauda da Sudais wa zai ci wassan🤔* Aisha.....ta fito duniya ta fada wajen da take ganin gida ne........................... Ya kuke jin labaran yar mutan niger? ? ? Me ke hasalaku a cikin labarunta? Me kuke son gannin ta daukaka ko ta zurfafa a cikin labarunta???????????? *❣IDAN KA RAINA INDA KAKE❣* Na: *SAJIDA* *_LITATAFAN MARUBUCIYAR_* *_Duk Karyar kada_* *_Yar Mahaukaciya_* *_Neman na kaina_* *_Bani da zabi_* *_Daga tafiya daukar soja_* *_Idan ka raina inda make_* *🌈KAINUWA WRITERS✍🏼 ASSOCIATION*🤝🏻 ```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}``` https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation 4⃣3⃣ Tare suka fito suka nufi dakin Rauda da dan saurinsu domin Humaira an sha wani uban lesh baki mai adon ja an hakimce saman babar kujera sai dai fuskarta ba fara.a sannan bata daura dan kwalin kayan ba tana zaune tana jiran uban masu gida dan fara aiwatar da shawarar da kawayenta suka bata Dakin Raudat suka shige wanda suna shiga Rauda ta shige bayi dan yin wanka ita kuwa Hafsat ta bude bangaren tufafin Raudar Wata doguwar riga mai kalar blu wanda ya ciza har yana satar baki ne ta ciro ta ajiye gefen bed daidai ana kiran sallar isha.i dan haka ta dauki hijab ta saka ta tayar da sallah Har hafsat ta gama sallah Rauda bata fito ba dan haka sai ta yi zaune tana adu.a tana duba hanyar fitowar Rauda Bayan nan ma ta kusan wani minti goma kafin take fitowa ta daura tawul sannan ta sako hijab Zanninta ta daura ta saka riga ta cikin hijab dinta kafin take tayar da sallah, Sai da ta gama ta yi adu.arta ta shafa sannan ta mike ta cire hijab din ta mikowa Hafsat abin busar da gashi ta zauna kasa Hafsat kuwa ta zauna bakin gadon ta jona ta shiga busar mata da gashin kanta tana caje mata shi Mamakin irin baiwar cikar gashin da kuma tsayi ga baki gashin Rauda ko ita da ta shafi buzaye gashinta bai kai na Rauda tsayi ba, koda yake itace batai gashin mai tsayi ba yayanta har ya fita izgar gashi hakama idan tana kallon hoton yayunta da suka rasu suma har gaban goshinsu lumbuk, kasa hakuri ta yi ta ce" sis ku kuwa wani yare ne? Rauda ta dan sosa kanta domin zafin cazar take ji, ita kam ba dai son jiki ba bata son kwata kwata a taba mata kanta kuma itama bata taba shi dan bata son kitso ko cazar gashi, Rauda ta ce" Abana bahaushe ne, mamana ce buzuwa Hafsat ta gyada kai ta gama caje mata ta dan shafa mata mai kadan kafin ta tambayeta ra.ayinta yanda zatai masa Rauda ta turo baki ta ce" ki daurw shi kawai sister Hafsat ta ce" aa, ke da ga abinda kika dauki niya, to ina gannin kawai a bada kai da fata Kai kawai Rauda ta gyada tana hasashen abubuwa a kasan zuciyarta Hafsar ta gyara mata gashinta sosai ta daure shi a tsakiya ta sake shi ya bazu a gadon bayanta Mikewa ta yi ta je gaban miroir ta dauko hoda da jagira da jan baki mai ruwan kasa, Cikin nutsuwa ta dan shafa hodar, ta samu ta saka jagirar a idonta sosai ya shiga ta ajiye ta dauki abin jagirar mai dan macaji karami a jiki ta caje girarta, Bayan ta gama ta shafa wannan jan bakin kadan ta kara gyara shi da kyau Juyowa ta yi da niyar dauko kaya Hafsat ta miko mata rigar nan tana fadin please sis Ta yi kalar tausayi Murmushi Rauda ta yi ta karba Hafsat kuwa ta shige bayi tamkar zata yi wani abin ita kuwa dama ne ta bata ta shirya cikin nutsuwa Rauda ta gane yaren Hafsat dan Haka ta cire rigarta ta dauki turarukan dake kan sif ta fara daukan farin humura ta bude ta shiga shafawa a wajaje kamar haka: kasan wuyanta, tsakanin yan biyu🌚 da kasansu, bayan kunanta bayan ta saka auduga ta hoge dan ruwan wanka ciki da bayan, guiwar hannunta daga gaban, sai kasa du inda keda lungu a jikinta sai da ta shafa Tana gamawa sa humurar ta dauko deodorant ta daga hamatarta ta fesa sosai kafin take bari ta dauko pant mai ruwan rigar ta saka da bras mai siririn hannu wace ta yi mata dam a jikinta Rigar ta warware, rigar ta bugu laushinta har sosa hanu yake 🥳 domin auduga ce kada, Namaki take ba wani mugun kwaliya a jikinta, sai dai kawai zagayen wuyanta da wasu irin perle kananuwa sosai masu kalar zumuwa aman kyalkyalinsu na jifan ido aka zagayasu a iya nan kawai Bismilah ta yi sannan ta yi adu.ar saka sabon kaya ta saka rigar Juyawa ta yi wajen miroir tana so ta daidaita ta, sai dai me ja ta yi ta tsaya cike da mamakin irin yanda rigar ta karbeta Wato wuyan rigar irin mai bateau din nan ne wanda kafadu suke waje wuyan rigar kuwa ya rike damatsunnan hannu hakan ya baiwa yan perles din nan damar layuwa suna dan kyali mai daukan hankalin mutun Rigar gaba dayanta a matse take domin ta bi jikinta ne har kasa ta mugun fitar da halitar jikinta da yannayin halitar nata, hannayen rigar mamar ta boye cikin rigar tana kalon gaban rigar ta dan bayanar mata da saman mamarta sannan ta kara matse su ta kumburo su tamkar zasu fashe, hannun rigar ne kawai budade sosai sannan akai masa tsaga wato fant.. sai gashinta da ya hau rigar ya konta lumbuk Hafsat ce ta fito daga bayi sai dai ta ja ta tsaya ta shiga shoki tana dariya ta ce" matar yaya masha Allah, Rauda ta yi dariyar itama ta ce" gaskiya ba zan iya fita a haka ba, haba da kunya...bamu yi sabon da zan iya yawo haka a wajen nan ba ni ke kanki kunyarki nake da wannan kayan Da sauri Hafsat ta karaso dan kusan Rauda ta ce" haba ke kuwa kawas so kike ki dizga ni ko me? To meye a ciki? Mijinki ne fa da abokiyar zamanki, ni kuwa kanwar mijinki ce uwa daya uba daya fa, ba yara kanana ke da akoy a cikin gidan ba bale ki ce idan sun ganki da irin shiga haka yau da gobe abin na iya shafar tarbiyar su, kinga Allah ne fa yayi umarnin ki gyara dan ki birge mijinki idan ya ji dadi kina da lada mai yawan gaske a wajensa, ki kasance mai kokarin samun yardar mijinta mai kara kusancinta da mijinta kin ji? Rauda ta gyada kanta a kasan zuciyarta kuwa ayannawa take" ya Allah, daman aunty Aishanama haka halayenta yake, da na tabata ba wanda zai ji kan mu du duniya kai ko iyayen mu, zamuna kashewa ne mu bine abinmu, Hafsat na da kyakyawan hali domin tana sowa dan uwanta abinda take sowa kanta, tana iya kokarinta dan kare kalmar imanin dayanku ba zai cika ba har sai ya sowa dan uwansa abinda yake sowa kansa Mikewa Rauda ta yi cike da kwarin gwuiwa ta kara fesa wani dan.karamin turare mai sunna bonbon ta shiga wani sanyin kanshin mai damkewa a zuciya A hankali ta bude kofarta bayan ta saka takalmi matar tudu sosai irin taka biredin nan kalar perle din rigar Suna kara kusanto palon suke jin muryar Humaira a dan dage tana ta kuka tana magana kamar haka" gayar kawaye ta yi husband suka hadu sukai min dukan nan, ka duba ka ga fuskana .... to haka shatin har bayana , ina zan saka raina? A ina ka auro matarnan? Ya kake so na yi da raina muna zamanmu ka kawo macen dake dukana har tana gayato mutane? Sudais dake zaune Humaira kuwa a saman kirjinsa sai murzarsa take tana bashi labarin Wai Mata ta gayato mutane an zo an yi mata duka kuma har ga shaidar abin a fuskarta wanda ya tabata a yada take da son jiki ba zata taba yiwa kanta hakan dan ta bata wani ba, a gaskiya yana cike da matsanancin mamaki, *MATA*? dama ta iya fada? Sannan a ina ta yi kawayen da zasu iya aikata irin wannan aika aikar? Shi dai a cikin binciken da Samir ya yi masa bai ma sako cewar tana da kawaye ba, to ko bai sansu bane bai tsananta binkciken ba, sam ba zai lamunci irin haka ba shi saima ya rabata da kawayen idan dai na banza ne domin fa ko halayen banza gareta ba zai iya rabuwa da ita ba dan haka dole ta daina, ya shaka fa sosai sannan Humaira ta bashi tausayi , ya tausayawa fuskarta abin shafe shafen nan ya sa abin du ya wani daukaka ya haye suntum Hafsat ce ta ja ta tsaya, tsoro karara ya bayanna a fuskarta Rauda da ta yi gaba kadan itama zuciyarta na bugawa tana mamakin wai ta gayato kawaye, ita? A ina aka yi? Wannan shine sharin da ake fada na kishiya ko me? ( ni kuwa nace hum Rauda sharin kishiya muguwa ai girma ne da shi ), Gannin hafsat ta tsaya ya saka ta dawo wajenta ta ce" lafiya? Hafsat ta yi mata kallon baki san yaya ba, ta ce" kina jin abinda take fada? Yaya baya son fada kar mu je ya dake mu gaba dayanmu Rauda ta zaro ido itama ta dan tsoratan aman ta dake ta ce" daga ta fada masa ba zai bincika ba sai kawai ya dauki hukunci? Hafsat itama kasa kasa ta ce" ai baya son fitina kwata kwata, idan ka jawo masa fitina yakan iya tataka ka ne, baya zama gari sosai aman du ranar da aka fada masa na yi izgili da wani baya bin sahun abin zai dake ni ne a wuce wajen Rauda da ta ji gabanta na tsannanta faduwa ta daure ta ce" zan dauki kasada, ki shige kicin ki dauko ragowar cake din nan sister ki taho da shi ....... Kafin Hafsat ta gama fahimtar me Rauda ke nufi kawai t ga Rauda ta dan daga kafarta da dan saurinta wanda nake iya kiransa da sauri mai hade da salo, bayan girgizar da halitar jikin Rauda ke yi nature ta kara da salo tana tafiyar sangartatun yara ta nufo falon gadan gadan aman a kasan zuciyarta tana ayana" shikenan Rauda shikenan kin gama yawo, lokacinki ne yayi kawai Rauda, mutumin da baya sonki? Shine zaki aikata wannan kasadar har ki je ya karya maki kafa? Ki koma abinki ki labe kinga kanwarsa da yake matukar so kanta tsoronsa take bale ke da kika diro basa daga sama Wata zuciyar kuma tace" ke haka zaki kare? Idan kin dauki iskancin yayarki ta zame maki dole ne, aman wannan kam ki nuna mata kema fa kin iya, yau ko zuwa makarantar islamiya da ta boko ya ci ace ka koyi yanda zaka zauna da mijinka , sannan ko baka da kawaye ko baka shiga gidajen mutane ko a gidanku mamanka ita daya ce a wawuya zaka tsintsinci abubuwa bale yayan zamani da suke binkitawa cikin hikima mai wayo na shanyewa dan gobe, ki jure ki je kawai du abinda ya faru ki dauka kan shinfida kike, sannan za.a ga ke da shi waye zai yiwa daya satar da bai shirya ba? Lumshe idannuwanta ta yi daidai lokacin da fitinanen kanshin turarensa yayi mata dirar mikiya cikin hancinta ya sakata sauke ajiyar zuciyar da bata shirya ba A hankali ta furta " tawakaltu alaLah Rauda ta shirya ta shagwabe fuskarta sosai, ta dan mumurza idonta kadan ta bude bakinta da wani irin salo na rigima ta fado falon ba tare da ta yi salama ba, Dan kukan shagwaba ne take yi da gangan tamkar bata gansu ba ta shiga dan kai kawo ta gabansu tana mugun jijiga jikinta tana hadawa da dan tsale tana kukan shagwaba Tunda ta afko falon nan Sudais ya dauke wuta ,, binta kawai suke da kallo wanda ita Humaira mamaki ne take wata sabuwa an cewa kare dan daudu, shi kuwa kiris zaka taba jikinsa ya biyoka , a zaunen dai yake aman ya afka wata duniyar, yama manta cewar ransa ne a bace yana shirin yin hukunci, haka kawai saukar hukunci ya sauko daga sama ya fado masa haka Daidai lokacin da ta dan didira ta dan bura tana kukan shagwabar nan shi kuwa ya kankame Humaira dake jikinsa wanda ya ji kamar zai suma kuma a fili ya furta " Wayo Allahna Humaira ce ta juyo da sauri ta sauke kwayar idonta a kan fuskarsa wada ta fara jan jaraba idannuwansa du sun kara girma sun yi jajajir da su , du uban ac din dakin zufa ta gani saman goshinsa Da bacin rai ta janye jikinta wanda hakan ya farkar da shi ya shiga murza yatsunsa yana jin yanda zuciyarsa ke yi masa fat fat fat fat ita sai ta rungumo Rauda ta rufe bakin nan nata ko ta samu nutsuwa Kasa jurewa yayi ya mike tsaye ya dan nuno yatsarsa ta kusan babar da yannayin ya jigata ya ce" *MATA, FA, ke ko? Ke ko? Menene ? Wa ya saka ki kuka?* Rauda ta turo lebenta na kasa, a kasan zuciyarta kuwa wani irin faduwar gaba da shaukin wannan yannayin take ji, haka kawai ta ji bata jin tsoronsa, kalonsa take irin na cikin idonnan , ji take tamkar tana yawo a gajimare a wannan lokacin , sannan ta jita gaba dayanta tamkar wata yar karamar baby yar wata bakwai a gaban mamanta Sosai ta kusanto shi, hakan ya bashi damar jin kanshin turaren da ta bulbulawa jikinta, ta kara shagwabe fuska ta nuno wajen da Hafsat ta yi mutuwar tsaye daria cike da cikinta, so take ta bushe da dariyar da sai ta fasa falon nan, yayanta ne? Wai dan Allah yayanta ne? Yanzu take na.am da matar da yayanta ta aura, ya ilahi ya manta abinda aka sako shi gaba ana fada masa , Kin fadin menene ta yi sai nuna hafsat da take cike da shagwaba da sangarta, Hafsat ta kwalalo ido, da idonta take girgizawa Rauda tanai mata maganar kurame ba ita ba Ta nuna Humaira, ama Sai Rauda ta yi mata murmushi kuma taki fadin nunawar na mene Sudais gaba daya ya rikice, yafa rikice, tamkar ba shine yayi alkawarin sai fa ta furta masa so kafin ya zube, sai dai kash ya zube din ne ba tare da an furta masa kalmar so din ba Nufo wajen Hafsat ya yi gadan gadan dan ya tambayeta me ke damun Rauda domin irin yanda take haskawar nan so yake ta haye kafafuwansa ta yi masa bacin nan, tana murmushi ta yi masa sangartar nan Muryar Humaira cike da bacin rai da hayagaga ce ta ce" Husband meye haka? Menene wannan kake yi? Sudais ya ja ya tsaya, zuciyarsa ce ta ce" Kai? Inalilahi, Sudais farka farka farka kafin ta karanto sirin zuciyarka ta yi anfani da shi ta halaka ka, Sudais Farkaaaaaaaaaaaaaa! Mutumin da ya tatara gaba daya hankalinsa wajenta sai ya juyo girar sama hade da ta kasa, sai da yayi da gaske yayi kundunbala da zuciyarsa kafin yake dawowa falon Rai a hade ya ce" ke! Ki natsu ki daina tayarwa mutane hankali! Cikin kakausar murya yayi maganar wanda ya saka rauda ta yi tsit, ya rikide mata ya dawo mata wancen mutumin da take tsoro take shayi, kikifta idannuwanta ta yi tana mai binsa da kallo Ki daina kawo min shirme a cikin gidan nan, sannan gobe da safe inna nemanku ke da auntynki, na gane dan ban zaunar da ku bane har batanci ya fara yaduwa a cikin gidana, ke ana tausaya maki aman har kece da kawo kawaye gida ku rufun mata ko? To ba dani ba! Ba zaku lahanta min *Matata* ba kin ji na fada maki *MATA* a gaskiya zan iya cewa tunda take da shi baganarsa bata taba yi mata ciwon na yau ba, ya haka ya fara yaudararta sai da ta fara kokarin karanto lamarinta na birge shi ya wulakantata haka? Ya kama maganar matarsa, ya nuna mata matar soyayarsa ta fita matar sadaka, *ke matar sadaka, na ji datijon ya ban tausayi na karbi tayinsa ya aura min ke kyauta* wa.innan kalaman suka daki zuciyarta tamkar yanzu take karantawa, hashi yanzunma ya tabatar mata ya kuma bita mata karatun wato daban take da dayar A hankali ta juya ta bi ta dayan bangaren kujerar ta zagaye ta fice da sauri ta nufi dakinta ba tare da ta nuna fushi take ciki kuka take yi ko hankalinta konce yake Da ido suka bita har ta shige, da murna humaira ta juya idauuwanta ta juya ta nufi dakinta itama dan sanarwa Kawarta ta ci galaba sannan ta fada mata irin barikin da Raudar ta yi ya gwaleta🤔 Bayan tafiyarsu, Sudais ya dago ya sauke jajayen idannuwansa kan Hafsat, so yake ya fada mata ta je ta rarasar masa MaTa , so yake ya fada mata ta cewa MATA ta yi hakuri aman ya kasa, shi fa kamanta adalci ne yayi, dole ya kawar da kansa tun kafin ya fara da ya sani A hankali ya zauna saman babar kujerar ya afka duniyar tunani yana jin wani irin ciwo a zuciyarsa yana jin yannayin da take ciki sosai a jikinta da zuciyarsa yana jin tamkar ya dawo da lamarin baya ya kasance yana shigowa bai tsaya ko.ina ba ya shige dakinta ya ga wannan rigar a jikinta, dan murmushi yayi kafin ya ce" Kampanin kulley ashe haka kayansu ke keruwa? Sai na karo mata dayawa da yawa.............. Tunda ta shiga ta rufe dakin yanda ba wanda zai shigo a hankali ta je ta zube nan kasa ta rufe idonta Sauraron irin dokawar da zuciyarta ke yi wanda ta fasara hakan da dan an yi mata wulakanci ne, Ta jima tana sakawa tana koncewa, daga baya a fili ta ce" Ke Rauda, sai me? Dan yayi maki haka sai me? Da ace ma wanda kike so ne da sai ya dame ki aman mutumin da kun tsani juna ke da shi?? Mikewa ta yi tana yarfe hannu irin sai me, kafin ta murguda bakinta ta shiga kokarin zame rigarnan ko ta walala da ranta Tana zage zio din rigar ta kallo waje daya ta bata rai a fili ta furta" wai *MATATA, MATATA MATATA!* ta karasa tana mai daga muryarta da irin abin na dukanta....... 🤣🤣🤣🤣 Raudancy love🤣🤣🤣🤣 *❣IDAN KA RAINA INDA KAKE❣* Na: *SAJIDA* *_LITATAFAN MARUBUCIYAR_* *_Duk Karyar kada_* *_Yar Mahaukaciya_* *_Neman na kaina_* *_Bani da zabi_* *_Daga tafiya daukar soja_* *_Idan ka raina inda make_* *🌈KAINUWA WRITERS✍🏼 ASSOCIATION*🤝🏻 ```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}``` https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation 4⃣4⃣ *na fans grup IDAN KA RAINA INDA KA KE, sabon tsari gabannan shine sai kun karanta kun more sannan a yada pagessss.......* Yau kwanan Aisha hudu a gidan su Sarah, sai dai tamkar ta shekara a cikin ukubar rayuwa ne, abin al.ajabi, abin mamaki, halin kananta wanda bata gani a gidansu ba, kai du safiya ta Allah sai ta ji muryar mahaifin su Sarah ya zo ya wanke mahaifiyarsu tas da mugayen kalamai har yayi mata burgar yana iya sakinta ya auro yar shila ita kuwa ka ji muryarta tana ta yi magiya tana dukawa tana rokon ya yi mata rai kar ya saketa, sai ya kama sunnayen iyayenta ya luluka masu ashar ya ce sun hada shi da masifa kafin wani lokaci ya dan cajeta kudi tukun ka ji ya tafi abinsa...... da safiya ta yi ta cakare ta fito falo da yan fadarta da sangartaciyar yarta a zauna a yi yinin yada habaici wa kishiyoyinta Yau kam tun wajajen karfe hudu na asuba kake jin yar hayaniyarsu, Firgigit Aisha ta farka daga saman salayar ta tashi da sauri zaune Tantar dakin da fitila domin Sarah tsoron kashe fitila take wai idan ta kashe mutun take gani yanai mata gwalo🤔 (rashin adu.a) Abubuwan da ta hango kusan Sarah ya saka ta yi gagawar kawar da kanta gabanta na tsananta faduwa Idan baki barni na yi ba sai na kaurace maki na shekara sannan sai na fadawa kishiyoyinki cewar bana zuwa shinfidarki Muryar baban su Sarah ce ta karade falon domin shi a rayuwa kwata kwata bai iya magana ta sirri ba, Saurin rintse idonta ta yi, jin muryar aunty tana fadin" ka ga ka rufa mini asiri, al.ada fa nake elhaj? Gashi kai ba ruwanka a haka zaka ce zakai idan fa da rabo sai na sami ciki cikin jini Wata shegiyar dariya yayi ya ce" ciki fa, ke yaushe rabonki da ki ji kukan jariri a gidan nan? Haka kawai kartin banza na zuba ku a gida na ciyar da ku, daga na rabe ku da sunnan hutu ko nutsuwa sai a fara amaye amaye na rainin hankali, zaku gane ne Da sauri ta saka hannayenta ta cushe kunnayenta, a hankali ta shiga maimaita na shiga uku, na shiga uku, menene wannan? Ina ne na fado haka? Tunda nake, tunda muka taso bamu taba jin ko gannin alamun irin haka a wajen iyayenmu ba, duda dakinsu daya basu taba nuna mana alamun hakan ba, wannan murya a bude basa tsoron Sarah ta ji su??????????????? Du yanda ta kai ga rufe kunnenta sai da ta ji komai a kunnenta, a karshe dai du najasarta sai da ta amince dan kar ransa ya bace ya aiwatar da abinda ya fada ya saka ta damuwa cikin kishiyoyi (wato ta take fadar Allah ta faranta ran mijinta dan kar tata rayuwar ta shiga wani hali😌.... to muje zuwa mu ga .....) Tun daga lokacin bacin ya kaurace a idannuwan Aisha, Gari na wayewa bayan ta gama sallah ta koma gefen bed ta dan shiga tayar da Sarah Sarah ta juyo ta saki mika ba salati ba adu.ar farkawa daga baci ta kalo wajen Aisha ta kashe mata ido daya kafin take saka hannunta ta cire abinda ta yi masha.arta da shi a jiya a jikinta ma take kwana da shi kuma a gavan Aishar ta cire ta kara gyara konciyarta dan komawa bacinta Aisha bata dadara ta hau gadon da kyau ta tausasa murya ta ce" haba yar uwata, ki tashi mu yi magana mana Sarah ta kebe baki a ranta ta ayanna zaki ci ubanki ne aman a fili ta ce" ina jinki ai Aisha ta ce" sarah ki ji tsoron Allah, abinnan da kike ya huce misali, kina dabi.a irin wace ba ta musulmai ba ko a yahudawan ba kowa ke irin haka ba, masturbat@ da kike yana da baba matsala ga rayuwar dan adam , zaki gurbata rayuwarki ne kuma ki je ga Allah ki hadu da azabarsa , Sarah rayuwarnan duka ma nawa take? Idan kika yi hakuri kika yi aurenki komai sai ki cikin nutsuwa tare da mijinki ga lada ga konciyar hankali kinga kuwa jin dadi dole zai tabata a gare ki, aman kina wannan abin tamkar karuwa Sarah ko kunyana bakya ji a gabana ???? Sarah ta mike ta yaye bargonma gaba daya ya kasance halitar jikinta ta bayanna idan ka ga mamarta tamkar macen da ta shayar da yaya uku kuma irin mai nonon nan mai lalacewa , sun nuna cewa wahala suke sha harda ta mamaki, Murya sama sama sarah ta ce" ka ji mini jaraba ina zamana a gidan ubana an zo ana fama a caza man kwakwaluwa! Aisha cike da tsoron kar mamanta ta ji muryarta sama sama haka ta zo kuma ta ga abinda take yi murya kasa kasa ta ce" ba haka bane Sarah, ki sasauta muryanki kar mamanki ta ji mana.... Ai kamar daga sama, kamar da wasa Aisha ta ji saukar mari a fuskarta daidai nan mahaifiyar Sarah ta shigo wato Aunty tana tambayar lafiya? Domin maganar sarah sama sama sosai ta yi, ita kuwa auntyn tana tsoron aban sarah ya dawo ya ji haka ya tambayi da wa take fada kuma kilu ta jawo masu bam Sarah cikin bacin rai bata rufe suturarta ba ko dan kunyar mamanta ta ce" ke har kina da bakin kiran wani karuwa? Gaki karuwa? Ai wanda ya guji iyayensa, ya barsu dan kawai suna tsawatar maki bama wani mugun abin suke maki ba ai ke kika nuna halayen karuwai, ke da *KIKA RAINA INDA ALLAH YA AJIKEKI* kike tatawa iyayenki hauka har kece mai bakin yiwa wani wa.azi? Ke sarah wai meye? Ba zaki sasauta muryanki ba? Aunty ta fada tana so Sarah ta sasauta haka Sarah ta ce" tunda ta zo , a daren da ta kwana a dakinnan sai da ta shiga rayuwanna, na yi mata iyaka da rayuwana aman ta ki, wai yau harda ce min na daina masturbat@ ba kyau waye waye, dan uban ubanta mai datin hula na taba jikinta ne? Sai da nace karta shigan man dakina aman kikq ce ta shiga na dan lokaci ne, ta fita a hanyana idan kuwa ba haka ba zan yi yanda Elhaj zai ji kowa ma ya huta! Tana gama fadar haka ta sauko gaba dayanta zindir kafin take jawo tawul ta daura ta juya dan zuwa yin wanka inda abubuwan lalatarta suka bayanna a fili saman bed din , Har zata shige ta ja ta juyo ta ce" mom, dan Allah ki daina yi masa gardama kema kuna hana min baci kawai ki ringa yi masa biyaya wai ba mijinki bane ni? Tana gama fada rmta fada daki Aunty ta juyo wajen Aisha, Aisha dake tsaye tana kikifta ido dafe da gefen fuskarta, ita wly mamaki da tsoro sun hanata yin kukanma, kai daman uwar Sarah ta san tana irin abinnan ko dai bata san exactement abinda ake nufi ba? Kina ji Aisha, kawai ki kawar da kanki, ki daina shiga sabgar Sarah, nima abinnan nata na damuna aman akoy wani malami da take karbar magani a wajensa ya tabatar min sannu a hankali sai ya kasance ko ance Sarah zo ga namiji ta suma dan tsoron zina sai dai mijin aurenta, Kin ga tana da saurin hawa, ni kaina a sannu nake kwatanta mata abinda ba kyau dan haka kar ki kuma yi mata magana wai dan kin ga kawai tana haka a hankali zata daina ai ba wani abin tashin hankali bane kin ga kar ranta ya baci ta hadani da abanta daga ke har ni din mu fuskanci wulakanci Aisha kwalalo ido ta yi, a ranta take ayanna" ta sani, walahi ta san abinda yarta ke yi, kai wannan wani irin gidanne ne haka? In sha Allah yau yau din nan zan fita na je na samu Rauda ta kashe auren sai na koma gida na ba su Mama hakuri sai su aura min shi hankalina ya konta (baki likiru ba🤔) Haka Aunty ta yi ta yiwa Aisha zanceceku masu shige da kashedi da gargadi kan Yarta kafin take mikewa ta fice a dakin ta kuwa sha wani arnen shada da mahaukacin dinki idan ka ganta tamkar matar sarki Tunda ya yi masu tsawar nan tafiyar dole ta taso wace dole zai je kwana biyu ne zai yi ya dawo hakan ya sa bai tara sun ba kamar yanda ya kudurta Hafsat ta yi iya yinta dan kawarwa da Rauda abinda Sudais ya yi mata a gaban Humaira, Rauda kam ta dauka sai dai ta kudiri aniyar sai ta saka Sudais furta mata kalmar so kamar yamda ya yi ikirarin matarsa, wato matar sonsa, itama ta karanta dan baya sonta ne irin wulakancin nan ke faruwa, zata yi iya yinta ta haukata masa zuciya a kanta kafin ta barshi, ko shi waye sai ya sota komai taurin zuciyarsa sai ta kaishi makurar da zai kasa jurewa har ya fada tarkonta mai shegen zurfi da zata gina masa, ita ta san takun da zatai masa, zata je ne da yannayin yanda ya zo mata rainin nan da aka yi mata ya kasance na karshe Yana gama al.adunsa kamar yanda ya saba ya zo baban falo ya zauna ya umarci Hafsat da ta je ta kirawo masa matansa Kamar kulun yana cikin shiga ne irin ta larabawa, ya kashe iya kashewa ya hade cikin shiga mai fuzgar du wanda ya kyala ido kansa, maza zasu furta masha Allah, yan mata zasu ayanna daman dama.... Hafsat ta shaidawa kowa, bayan ta fito ta sanar masa ta nufi dakinta dan kontawa ta basu waje su tatauna Sai a wannan lokacin Rauda ta shiri shiryawa, ta canza kayanta zuwa dogon wando da rigarta top ta dora doguwar rigar abaya fara kar mai hasken gaske sannan ga shara shara ce domin kayan kasan ana gannin komai Farin dan kwali ta dauko ta yane kanta kafin take saka silifas baki wato irin kananan kayan ta dauko wayar wajen Hafsat dake hannunta tana dan jujuyata ta fito ta tunkaro falon Humaira kuwa tunda ta ga fitowar Rauda ta kontar da kanta saman kirjin Sudais tana dan yi masa magana kasa kasa tana sakin murmushi wanda maganar bama na murmushin bane kawai dai yi ne dan tana nuna ta isa , irin burgar nan a gaban kishiya A zuciyarta Rauda take ayanna ke ya dama, da ace ina sonsa ne bakin cikinki zai kashe ni Tana karasowa zama ta yi kujerar dake facing din su, ta tsare su da ido irin kallon nan na gani kashe ni Cikinsu shi kadai ya iya amsa salamarta shima can kasan makoshinsa sannan ya hana kansa kallonta dan gudun matsala A hankali ya tayar da Humaira daga jikinsa ya gyara mata dan kwalinta murya kasa kasa ya ce" ki koma kusa da yar uwarki ina so ku bani hankalinku Sai da ta yi yangarta kafin ta mike ta nufo dayan kujerar ta zauna su duka suna kallon sa Sai a wannan lokacin ya dago da kansa ya ce" asalamu alaikum Kamar yanda ya amsa salamarta itama ta amsa wanda ba dan ya kafe lebenta da ya sha man lebe yana ta kyalkyali ba da ba zai ga amsawar nata ba Dan murmushi yayi a kasan zuciyarsa ya ayanna wato ta rama Gyaran murya ya yi kafin yake dago da kansa ya ce" mun taru kasan innuwa daya ne dan bautar mahalincinmu wanda yayi umarni da mu raya sunnar mafi soyuwa a wajensa wato annabi muhamadu salalahu alaihi wa salam, Dayarku ba zata fi daya a wajena ba sai wace ta iya zama da ni, ta iya kare hakokina, ta iya hakuri da halayana, ta iya riritani tamkar kwai ta shagwabani ta nunan na fi lumfashinta mahinmanci a wajenta, to ina mai tabatar maku nima zan faranta mata fiye da tunaninta, ya karashe cike da gadara inda Rauda ta bude dara daran idannuwanta tanai masa kallon mamaki domin yannayin yanda yake maganar dole ka yi mamakin irin wannan shagwaba, ita walahi kunya ma ta ji ta dirar mata wai ya wani matse baki ya ce " ta shagwabani, aa a goyaka dai Du ita daya ke magangannun nan a zuciyarta Ci gaba yayi da fadin" Dolenku ku nunan soyaya, dole ku furtan kalmar so domin shi ya hada mu..... ya karashe yana mai sauke idannuwansa cikin na Rauda Ya kara shagwabe fuska ya ce" dole mace ta so ni dolenta ne!🤨 Sada kanta ta yi a ranta ta ce" toh fa, kaji sabuwa an cewa kare dan daudu, wai daman shi haka yake , A hankali ya kai hannunsa kan sajensa yana dan shafawa ya ce" matata marigayiya ta kasance idan na yi fushi tana shafa man gemuna tana shafan kirjina tana rarashina har na yi barci saman cinyarta, Allah ya jikan mata Ido Rauda ta kuma zarowa, a ranta ta ce" lale na jinjina mata, wannan gabjejen katon take iya wani rungumarsa lale ma, shi kuwa ko kunya ya wani zo gabanmu yanai mana wannan zancecekun na iskanci mts an ji kunya Dan haka nake so ku nutsu ku daina kokarin tayar min da hankali kowace ta yi yaki da dukan karfinta dan samun soyayata...... ya wani karashe yana jan ta...... din yana dafe kirjinsa daidai saitin zuciyarsa yana kuma sauke kallonsa kan Rauda wace bata san gaba daya yawancin magangannun yanai mata nuni ne da ta furta masa kalaman soyaya Sai maganar baya, kwana nawa mawa kuka tsara za kuna yi ? Humaira ta dago da mamaki ta sauke kallonta kansa , da gaba daya bata baiwa magaganun nasa importance ba domin ta san shi din namiji ne irin masu son shegiyar shagwabar nan wajen matayensu abinda ita kuwa a gaskiya ba zata iya ba garjejen kato yana yi mata shagwaba, sai dai yanzu wai raba kwana, a mamakance ta ce" raba kwana kuma? Sudais ya hade fuska ya kalo wajenta ya ce" eh da damuwa ne? Humaira ta sada kanta, a ranta fadi take kan uba, kwana zai raba mana da yarinyar nan? Wai ni ya aka yi nake mugun jin kishin yarinyar nan fiye da Khairath? Me ya sa ta tsaye min a kahon zuciya ta hanani samun sukuni? Ina ba zai yiwu ina ji ina gani ya raba shinfida da yarinyar nan? Wannan mai shegen fi.ilin? Sai dai lumfashina ya rabu da gangar jikina da na bari ka rabeta *ku nake saurare* cewar Sudais yana kallon su Gannin Humaira ta ki yin magana ya sa Rauda cikin kontaciyar murya ta ce" ni kam ba sai an raba ba, na yafe A tare suka kallota, Sudais ya zabga mata hararar da bai san ya iyata ba, muryarsa a dake ya ce" na raba maku kwana bibiyu daga yau, sannan ina mai nanata maku zaman lafiya a gidana , bana son fitina ko kadan Yana gama fadar haka ya mike yayi gaba da haushin Rauda" *Na yafe* wai ta yafe, to ki je ki yi ta yafewar ni naki na yafen yar bakin ciki marar wayo, yanzu na gama nuna maki ki fadan kina sona shine dan baranci kika nunan ma bana gabanki, to ni ban yafen ba *naki na yafe Life* Sowi nah😌 *❣IDAN KA RAINA INDA KAKE❣* Na: *SAJIDA* *_LITATAFAN MARUBUCIYAR_* *_Duk Karyar kada_* *_Yar Mahaukaciya_* *_Neman na kaina_* *_Bani da zabi_* *_Daga tafiya daukar soja_* *_Idan ka raina inda make_* *🌈KAINUWA WRITERS✍🏼 ASSOCIATION*🤝🏻 ```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}``` https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation 4⃣5⃣ Haka yayi ta mita kafin yake zuwa dakinsa ya cire kayan da ya saka ya dauki tawul baba ya nufi bayi, Yana shiga ya tara ruwa a bahon wankan kafin yake shiga ciki Ruwa ne masu dumi hakan ya bashi damar lumshe idannuwansa, a kasan zuciyarsa ya ce" du wankan da nake bata taba nuna irin yanda wasu matan ke yi min ba wato su tsareni da ido tamkar sun ga sabuwar halita , su kafe ni da mayatacen kallo wani lokacin har ya kasance na tsargu........ Ya aka yi tsarin halitata bata fuzgarta kamar yanda take fuzgar yawancin matan da na hadu da su a duniya? Ko dai bata da feeling ne? Ko tana cikin matan da basa soyaya ne? Wani dan murmushi ya saki, ya ci gaba da fadin" karya, karya ne, ko bakya soyaya sai kin so ni, haba *MATA* ki gane mana, kema ki maida hankali mu fara cin soyayrmu kar mu shiga hakinta, so fa baya son jira Wani murmushin yayi yana dago hannunsa cike da kunfa ya kai daidai kakauran kirjinsa wajen zuciyarsa ya ce" ke, shigarki na bambanta abinda kike furtawa, shigarki da kike yi yana fasara ki a abu uku wanda ni nafi son dayan, na farko idan aka ga budurwa sabuwar amarya ko wace bata da aure musulma a kasarmu ta hausa na irin shigar nan sai a yi zargin bata jin magana Na san kina jin magana ko Mata? Na biyu mace a gidan mijinta, ya kasance tana irin shigar nan tana baza kanshi tana taku mai dauke numfashi akan fasarata ne da wanda ke son ta ja ra.ayin mijinta ta kara dankon amincin dake tsakaninsu ya kasance muradinsa .......ne🤣, Lumshe ido yayi a fili ya furta" Wayo MATA, Allah amen wannan nake so😊 Sai na uku akoy mutanen da su rayuwarsu kennan bukatarsu ce hakan ya kasance su dai jin dadinsu su gansu cikin kananan kaya, Ya yatsina fuska kafin yake mikewa da mousse din jikinsa ya dauko tawul ya goge jikinsa da kyau ya fito ya je saman bed dinsa ya saka wandonsa wanda ya dara gwuiwarsa ya kure gudun ac ya yi konciyarsa Ta jima tana sakawa da warwarewa, Tana matukar son ta ga iyayenta, tana son ta gansu ta fadawa abanta wanda ya aura mata, tana da bukatar shawarar mutun mafi kusanci da ita, Can ta lumshe idannuwanta a fili ta furta" Aunty, kina ina? Kina ina ne aunty? Ina fatan kin yafe min, ki gane kowani bawa da tasa kadarar, aunty ki daina son *MIJINA* Shiru ta yi ta zarro ido, maimaira kalmar mijina ta yi, can kuma ta saki murmushi, a fili ta furta" Rauda kin kirayi Sire da mijinki hakan na nufin kin karbe shi ne a matsayin mijin naki? Tamkar zarariya ta ce" dole na daukeka a matsayin mijina Sire, ka san wani abu? Da ace ka zo min ta wata hanya to zqn iya baiwa zuciyata damar amincewa da kai, da sai na bata damar *son ka* , (ni kuwa na ce da mutun zai iya hanata ko ya sakata soyaya da ba haka ba) Ci gaba Rauda ta yi da zancencekunta tamkar zarariya, takan saki kayatacen murmushi har Hafsat ta shigo suka shiga game a wayar Hafsat din Bayan tafiyar Hafsat magariba ta sanyo kai, Rauda sai tiri tiri take a dakin ta kasa zama, Ji take bukatar gannin iyayen nata na kara daukaka a zuciyarta Dakin da yake malakinta ta shiga bi da kallo, Kafin take hasaso gidansu Ya salam shi ne abinda ta iya furtawa Ta sani sarai aunty Aisha ba zata yi wani abu dan jin dadin iyayensu ba sai dan nata ita kanta, kudin aikin da suka yi ko ta je ta biya kudin makaranta , A fili ta furta" Abana, mamana a wani hali kuke ciki? Hankalinku a konce yake kuwa? Kuna samun abinci? Kuna kwana a cikin gidan sauro? Aba ka daina kwana saman tabarmar? Mama kin kontarwa da Aba hankali? Kin yi hakuri kuna zaune lafiya da Abanna? Ku yi hakuri da yanda rayuwa ta zo mana, Abana mamana zan ci gaba da aiki ko dan na dauke maku nema, in sha Allah kuma zaku ji dadin rayuwa Mamana, in sha Allah sai kakannuna sun yi mamakin tsatson malan Ahmad ce haka? Ba zan dogara da Sire ba, ba zan taba zuba ido a nasa ba, zan nemo mana namu ne na ringa sayo mana shinkafa yar gwamnati, maka kifi nama magi muna morewa, Ta saki murmushi kafin take dauko zumbulelen hijab dinta ta fito gadan gadan ta nufi dakin Sudais Fitowarsa kennan daga wani wankan ya hangota tsaye tana danna soneri dan neman izinin shiga Murmushi ya saki nan da nan ya ji shi sakayau gajiyar bacin du ta ware, Wani dan dira yayi kafin yake kara daure tawul din jikinsa da kyau ba tare da ya raba wani abin ba ya nufo kofar ya danna butom din budewa ya budu Bayannuwarsa a gabanta kawai ta gani, gabjejen halitarsa mai firgitarwa ta yi arba da ita Rauda bata san lokacin da ta dora hannunta saman kanta ba ta ce" Wayo Allahna , Da gudu ta juya dan tserewa sai dai ta makaro domin Sudais ya rikota taf a hannunsa Tamkar jaririya ya dauko da kafarsa ya rufe kofar ya nufi cikin dakin da ita Tabas da Rauda na jin fitsari da ta sake shi a wannan lokacin domin contact din jikinsa da abin ruwa da firgitar daukotan da yayi sannan bata gama tsoron ba ya kama hijabinta ya ja a hankali ya nemi cirewa ba alamun wasa a fuskarsa Wani irin ihu ta.... *❣IDAN KA RAINA INDA KAKE❣* Na: *SAJIDA* *_LITATAFAN MARUBUCIYAR_* *_Duk Karyar kada_* *_Yar Mahaukaciya_* *_Neman na kaina_* *_Bani da zabi_* *_Daga tafiya daukar soja_* *_Idan ka raina inda make_* *🌈KAINUWA WRITERS✍🏼 ASSOCIATION*🤝🏻 ```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}``` https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation 4⃣6⃣ Ihu take tana rike hijabin shi kuwa yana kara matsawa kusa da bed Sai da ya karasa sosai kafin yake cire mata hijabin gaba daya sannan ya ajiyeta saman bed din Tamkar an jona mata lankatarki ta yi wani irin juyi sai gata a tsakiyar bed din tana zaro idannu tana kallonsa da mugun mamaki da tsoro Murya na rawa ta ce" ba haka tsakanina da kai sire, dan Allah kar ka yi min haka Sudais ya kafeta da ido, hawa yayi saman bed din shima muryarsa da wani irin amo ya ce" me fa? Menene bakya so na yi maki? Rauda ta sada kanta kasa tana wasa da yatsunta gaba dayansu sannan jikinta na bari sosai Ina sauraron ki, Sudais ya maimaita yana kara kusanto kansa da ita Baya ta ja sosai har ta hade bayanta da bed, ta yi irin zaman nan na tsoro Binta yake da kallo, a zuciyarsa yake ayanna " dalilinta na tare a nigeria , ina faman yin watani Ni ni ba komai ba ..... Rauda ta fada tana turo bakinta tana kara matsawa kusan kan bed din Sudais ya dan yi murmushi ya mika hannunsa ya kamo hannunta na dama Ido ta zaro bai bata damar yin magana ba ya jawota da dan karfi wanda hakan ya sa ta taho luuuu gaba dayanta ta sauka a kirjinsa domin nan yayi mata masauki, A hankalu ya juyar da ita ya kasance ta bashi baya ya sakata a tsakiyar kafafuwansa ya kasance gadon bayanta jingine da kirjinsa mai yalwatacen gashin kirji da girma , Abin wankan nan da yayi ya sa jikinsa ya yi sanyi ga sanyin ac A hankali ya sako hannayensa ta cikin cikinta ya dan shiga shafawa kafin yake kai hancinwlsa wajen wuyanta ya shiga shinshina Mamaki, da wani irin nutsuwa ya ji na sauko masa kafin a hankali yannayin jikinsa ya fara canzawa Murya kasa kasa ya ce" na zata shi ya kawo ki? Ai ni idan an zo wajena nemansa ne kuma nakan yi iya yina dan gannin na biyawa mutun bukatarsa dan ina gudun hakin mutane Gaba daya ji take tamkar yana bin jikinta yana saka mata wani abin da bata san da shi a duniya ba, feeling, feeling ne na tashin hankali ke sauko mata, ba dai wani abin yayi mata ba aman gaba daya ta rikice tana neman fita a hayacinta A cikin kunnanta yayi magana wanda shi kansa ya fara hawa layi, laushin damatsunnanta da hannunta da ta kawo saman nasa da niyar bambare shi daga jikinta aman ta kasa sai ma ya kasance ta shiga shafa hannun maimakun bambarewar, sai yannayin kanshinta da shima bako ne a wajen sa, iya wuyanta da wajen kunnenta kawai ya iya sinsinowa aman ba karni, ba karni ko warin ruwa babu ko kadan baya ju a jikinta, Ji yayi ana sara masa kansa, a hankali ya fara sasauta rikon nata jin gaba daya jikinsa ya fara mumurdewa Ajiyar zuciya take saki a kai a kai tamkar ta yi tsere, da sauri ta shiga jan duwawunta domin ya cikata ya konta nan Tana sauka daga kan bed din ta aniyar tserewa sai dai gaba daya tamkar an zare mata laka , bata da karfi ko kadan a jikinta , Baki fadi abinda ya kawo ki ba Muryarsa a wani irin amon murya ya daki kunnanta A hankali ta juyo ta ga sai mamatse kafafuwansa yake yaki zama Kasa kalonsa ta yi domin sai take gannin tamkar ba shi ba, Kanta ta sada kasa , murya na rawa ta ce" dama , dama , na zo ne na tambaya yaushe zan koma bakin aikina? Bai san lokacin da ya bufe idannuwansa ba ya sauke mata kwayar idannuwan a kanta Gabanta ne ya yanke ya fadi sakamakon irin yanda ta ga kwayar idonsa sun koma jajajir, da sauri ta cire nata idannuwan daga nasa ta kuma sada kanta kasa Kallonta yake yana nazartarta, can murya kasa kasa ya ce" me yasa kike son yin aiki? Dago da kanta ta yi da dan mamaki,, wata zuciyar tace ba abin mamaki bane may be bai san cewa a gidanku ku biyu kawai iyayenku suks haifa, mata, wa.inda da Allah da ku suka dogara , da ya san yanda mahaifinta ke nema tun karfinsa da bai yarda ko da wasa ya yi mata tambayar me zata yi da aiki? Bata iya ce masa komai ba sai kanta da ta dan girgiza Ajiyar zuciya ya sauke , a hankali ya ce" zan yi nazari Juyawa Rauda ta yi ta fice tana adu.ar Allah ya cidata Wani wankan ya sako kafin yake zuwa ya shiga shiryawa yana yi yana duba agogon dakinsa Kansa ya dafe domin har an yi salar magarib an bar shi dan haka da hanzari ya dauki tapi ya shinfida ya shiga gabatar da Sallah cikin nutsuwa Bayan ya gama ya jima yana adu.a kafin yake mikewa ya shirya da niyar fita ya yi sallar Isha a waje sannan ya je anguwa Kayansa yake sakawa yana fadin" wato dai sai an daga maka hankali , aiki? Me zaki yi da aiki *MATA?* Tare suke da Samir tunda suka fito daga masalaci wajen meeting na manyan mayan yan kasuwa masu rike da kaso 60 na nigeria fannin talafi wa Gwamnati, suna gamawa Samir ya jawo motar wanda kira.a ke tashi sannu sannu Sudais ya ce" SAMIR, KAI NI GIDAN Su MATA samir ya juyo ya dan kallo shi, gidansu kuma? Me zai je yi gidansu? Ko laifi ta yi masa? Aa halayen Sudais ba irin na ya kai kara bane dan matarsa ta yi masa laifi domin ko mahaifiyarsa baya yarda ta san tsakanninsa da matansa dan yau da gobe sai Allah tana iya tsanarsu shi kuwa idan yana da bukatarsu a tare da shi a samu matsala Samir bai zame ko.ina ba sai kofar gidan su Aba, A daidai wannan lokacin Aba na zaune saman dan dakalin kofar gidan yana kallon gari haka dai yana dan nazarin duniya Sudais ya jima yana kallon gidan, da bangon gidan, sannan ya maido dubansa wajen Aba wanda kallo daya ya yiwa motar da ta tsaya a dan gefensa ya kawar da kansa , SUDAIS ya sauke ajiyar zuciya ya tina rayuwarsu ta da can baya su sun ma kasance masu rufin asiri, a hankali ya furta " *ALHAMDULILAH* Issa mai kanti ne ya zaburo ya zo kussan motar yana dan lekawa sai rawar jiki yake yana fatan Allah ya sa ta samu Ganninsa ya sa Sudais ya dan zuge gilas din motarsa kadan dan jin lafiya? Barka yalabai, Issa mai kanti ya fada yana yage bakinsa hakoransa suka bayana da jan goro futu futu Sudais ya yi murmushi, sosai rayuwarsu ta da take fado masa, suma sun zauna a irin anguwar nan, sannan sun rayu da irin mutanen nan , wani murmushin ya saki da ya tina majalisar su Abansa, yakan je ne tare da Abba dommin shi yana yaro ma akoy shakuwa tsakaninsa da Abansa sosai Hannunsa ya fitar ya mikawa Issa sukai musabaha, kafin yake fadin" Gidan MALAN AHMAD muka zo Domin ya san tsegumin hakan ya fitar da shi, kuma yana sane ya fada masa dan ya san zai iya buda baki ya ratafa masa magangannu yana son sannin datakun surukan nasa Lumfashi ya sauke kafin yake cewa" ina fatan dai ba yarinyar gidan ba kake so Yalabai? Domin dai kana hangensa can? Wannan shi ne Malan Ahmad, shi kam mutumin kirki ne, talaka ne da ya iya talaucinsa sai dai yayi shirme ya kai yayansa boko, yaran mata ne suka girma har suke kokarin tsofewa a gida tun ana bibiyarsu har ya kasance an janye domin shegen idon cin naira ne da su Ita karamar dai uban ya bayar da ita sadaka har wasu na cewa ko auren jari yayi wa yar , sai dai tunda aka yi auren yana nan yanda yake jiya i yau baya maganin naira goma sai shegen sabkon zuwa wajen Aiki Faskare *Faskare?* Sudais ya maimaita a hankali, Issa ya ce" Faskare ne sana.arsa, har an gajiya aman ba wata sana.ar sai shi Kai Sudais ya girgiza ya yiwa Samir nuni da ya salami Issa domin ya fara caza masa kwakwalwa A hankali yake takawa har kofar gidan su Rauda Yana zuwa yayi salama wa Malan Ahmad Aba ya juyo yana mai amsa salamarsa, Sai dai abin mamaki kafin ya mike Sudais ya zube kasa gaba dayansa kansa a kasa ya ce" Aba barka da hutawa Sai a sannan Malan Ahmad ya gane SUDAIS , ikon Allah daman a samari akoy sauran masu biyaya haka? Mijin Raudansa ne , Da sauri Aba ya amsa yana mai umartarsa da ya tashi ya tashi domin wajen ba dai dati ba , kun dai sani😌 Kin mikewa Sudais yayi sai da suka gaisa sosai da Aba kafin yake cewa" zuwa na yi daman na gaishe ku Malan Ahmad cike da jin dadi yake amsa Sudais, harma ya ce da shi bara ya fadawa mamanta ya shiga su gaisa Kafin Sudais yayi magana har Aba ya shige dan haka ya shiga dan shafa sajensa Shiga suka yi a tare inda Sudais yake dan bin gidan da kallo da yannayin hasken farin wata Tabarma mama ta shinfida kafin take takurewa can gefe ta zauna Har kasa itama ya duka ya gaisar da ita inda ya ji muryarta irin na Rauda Mikewa ta yi ta dauko masa ruwa a randa mai sanyin gaske ga kanshin laka ta zuba a kwanon silba na aba na shan ruwa ta kawo masa ta ajiye A nan hasken farin watan ya bashi damar gannin fuskar mahaifiyar abin kaunarsa Kamarsu daya shi ne abinda zuciyarsa ta ayanna masa Mama na so ta tambayi Rauda sai dai kunya da nauyi sun hanata yin hakan har Sudais ya mike ya tafi ba tare da ya ajiye masu komai ba (notez bien bai basu komai ba) Yana zuwa suka shige mota suka tafi da Samir yana ayanna abubuwa a kasan zuciyarsa Konci tashi yau an yi sati uku wanda a sati ukun nan zuwan Sudais gidan Su Rauda sau biyar Ya maida wajen wajen zuwansa ya zauna su zanta dan halin rayuwa da iyayenta harma ya ci abinda aka kawo masa ya tashi ba tare da ya basu ko naira biyar na alkhairi ba Abinda ya fara birge shi shine bai ga canji a fuskar su koda a wajen amsa gaisuwarsa ne (Nuna kwadayi ga abin wani, na sakawa ka zama hadamamen mai zalama) Yana karantar rayuwar iyayen matarsa cikin nutsuwa yana fahimtar abubuwa da dama A yau ya dawo daga gidan da ya saka ake gyarawa daya daga cikin gidajensa ya shigo a dan gajiye domin ya je ne ya ga irin tsarin kayan da aka zuba a gidan kama daga gadaje kujeru tv kayan kicin da sauransu Yana zuwa ya tarar da su zaune a falo suna game gardama ya kaure tsakanin su Ba zato ya zauna shima ya ce " a sake, a saka ta mutun uku Da mamaki suke kallonsa daga Raudar har Hafsat din Girarsa daya ya dage yana kallonta ya ce" sannan ni zan fara Au na manta, mama ta ce a gaishe ki, da ABA Da sauri Rauda ta dago tana kallonsa, muryarta na rawa rawa ta ce" mammmmamana? Sire Abannna???????? Tana fada ne tana matsowa kusa da shi sosai wanda ya dago idannuwansa ya sauke a kanta.......ya ce"""" *❣IDAN KA RAINA INDA KAKE❣* Na: *SAJIDA* *_LITATAFAN MARUBUCIYAR_* *_Duk Karyar kada_* *_Yar Mahaukaciya_* *_Neman na kaina_* *_Bani da zabi_* *_Daga tafiya daukar soja_* *_Idan ka raina inda make_* *🌈KAINUWA WRITERS✍🏼 ASSOCIATION*🤝🏻 ```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}``` https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation 4⃣8⃣ A hankali ya lumshe idannuwansa ya shiga lailaya lebenta kafin yake isa cikin bakinta, kanshin maclean na frz ne yake shiga bakinsa, idannuwansa ya kara lumshe kafin yake cafke lebenta ...... .. Sako yake bata iya nan, sakon da ya zo mata a rashin shiri sannan daga mutumin da take shayi........ bata taba kwatanta irin haka da kowa ba, bata taba kawo haka lamarin yake ba........jikinta ne ya dauki rawa ta damke damatsunan hannunsa ta shiga dan girgiza masa kanta dan ya tsayar da kissing dinta kar ta sume masa Elhaj Sudais Uban masu gida yau ya zama dan gida, ya mace ne a bukatar kara gaba daga nan domin lamarinta na zuwar masa da ba zata kala kala...... Bakin Mata kanshi yake fitarwa, wari bai dake shi ba Bakin mata laushi, haka jikinta.... gashin kanta kanshi ya salam...... ya salam....... Cikin nutsuwa ya kame bayan keyarta ya kara kusanta jikinsa da nata still yana kissing dinta ... Gani yayi tsayuwar bata yi masa a hankali ya cirata a jikinsa bai saki bakinta ba yayi bakin bed da ita A hankali yake kara sarafa harshensa da nata lumfashinsa na wani irin gudu Gannin Sire baya jin yarenta ta fashe da kuka tana kokarin cije lebensa Tsai yayi da abinda yake yi a lokacin kuma aka buga masa wani irin abu na tunani....yarinya ce, sai ta warware, sai ta zama bunkasashiyar budurwa zata iya da kai Sudais....ka bari kar ka tsorata ta mana ka yi hakuri da bukatarka gareta har sai ta isa daukan nauyinka Du kwakwaluwarsa ce ke yi masa fadan nan wanda a hankali ya samu ya shinfidar da ita saman bed din yana shafa gefen gashinta alamun rarashi Ajiyar zuciya kawai take saukewa idannuwanta a rufe domin kunyarsa take ji sosai(ki shirya fa) wai dama haka yake? A hankali ya mike ya daidaita mata gudun ac ya kuma dawowa kusa da ita ya duka sosai ya shafa gefen fuskarta murya can kasa ya ce" ki yi baci, kar ki yi tunani ki dauki rayuwa a yanda ta zo maki *MATA* Tsikar jikinta sai da ta mimike ta bi shi da kallo har ya mike ya fita a dakin nata Sudais na shiga dakinsa ya je ya yi wanka ya fito ya yi nafilarsa ya zauna ya yi adu.u.insa kafin yake mikewa a hankali ya hau bed Bashi da tunani sai nata, bashi da buri sai na kasancewa da ita... yana son a haka ya shigeta ba tare da ta ankara ba, ya kasance bugun zuciyarta wanda sai ta yi nisa da shi zata gane shi ne ita ita ce shi Yana begenta har baci ya daukesa Da safe bayan ta gama abinda ya zame mara al.ada wato gyaran dakinta, wankin bayinta, wanke bedsheet dinta... kafin take shiga wanka A wajen wanka a kadan Rauda na daukaninti goma sha biyar wanka kadai ba wani uzurin ta kasance mai kwalkwalce kwalkwalce, taba nan , wanke can, goge nan, takan hada ruwa har kala uku tana wankanta cikin kuzari kafi ta fito Abin busar gashi ta dauka ta busar da gashinta cikin nutsuwa kafin take shafa masa man gashi mai sanyin kanshi ta daure shi a gadon bayanta Yau kuma ta tashi da son saka kayan hausa dan gaka ta dauko wani lesh mai ruwan sararin samaniya (bleu ciel) da dan fari fari wajen adon....lesh din sabon fitowa ne, wato lesh din matan gwana😂, ya hadu ya hade an yi masa dinkin yan matan zamani riga wace ake ce mata makeba sai dai ba mai tsayi har kasa ba bakinta gwuiwa da zaninta da dan kwalinta Dinkin ya dinku dogon hannu ne da shi cigarette sai wuyan kuwa bateau ne ..(c tres joli l model) cikin nutsuwa ta shafa mayukanta na humra wa.inda suma a dakin aka jera mata domin Sudais ma.abocin kanshi ne Bayan ta shafa ta saka kananun kayanta pant nd bras kafin take daura zaninta irin daurin hausawa ya hau kugunta ya dauru da kyau ta saka rigar ta ja zip Dan kwalin ta konce ta dauko abin daurin dan kwali baki dogo na yayi ta kontar da dan kwalin ta saka ta gyara shi da kyau kafin take zuwa gaban mirror ta daura shi ya zauna dasss ta yi daurin zahra bahari aman bayan ta yi shi yayi tamkar bindin zakara kosashe Tana kokarin dauko sarka ya shigo dakin da salama a bakinsa Da mamaki ta juyo domin sam bata ji karar shigowarsa ba sai kuma abin jiya ya fado mata a rai wanda ta kwana tana tunawa ta yi saurin juyawa tana dan rurufe ido Murmushi ya yi ya shiga takawa cikin nutsuwa har ya karaso wajen sarkokin nata Wata yar siririya fara kar mai dan bul shima farin ne aman mai haske domin ana ganin cikinsa tamkar ruwa ne a ciki sai yan kunayensa siraru suma bakin kafada domin da dan tasayinsu ya dauko ya nufota yana murmushi Yana karasowa ya gyara sarkar ya sakota a hankali ta wuyata kafin yake balawa ya dan raba kansa da wuyanta sajensa ya shafi wuyanta ta lumshe ido Murya can ciki ya ce" morning *MATA* kunya ce ta sakata ta narke a kirjinsa na gaisheran da ya fara, bata iya amsawa ba sai kara lumshe ido da ta yi tana kara shigewa kirjinsa domin yanda sajensa ke hawan mata wuya sai tana jin tamkar yanai mata tafiyar tsutsa ne Murmushi ya saki, ya ce" wani turare ne kike anfani da shi haka? Idannuwanta dake lumshe ta dan bude ta kallo shi, Dan yatsanta ta nuna masa wajen da turaran yake Dubansa ya kai wajen tarin turarukan ya lumshe idannuwansa, a ransa ya ayanna lalai zai kara oder irinsu domin kanshinsu daban ne a jikin *MATA* Haka kawai ta rasa abin ce masa sai cewa ta yi" a ina ka koyi saka sarka wa mace? Tambayar ta bashi mamaki, wa mace? Aman sai ya kawar da hakan ya ce" ya dace mai sana.a ya iya sarafa abin sana.arsa *MATA* Du idan ya kirata da mata takan ji sunnan wani iri, ya aka yi baya kiranta da RAUDA sai dai ya kireta da sunnan mata mata mata ta dan kebe lebenta A hankali ya cikata ba dan ya so ba ya ce" ki shirya mu je ki ga mama da Aba Rauda ta kwalalo ido ta matso da sauri ta riko shi ta ce" dan Allah ? Zaka kai ni na ga mamana? Idan kika kuma cewa mamanki ke kadai za.a fasa Da sauri Rauda ta shiga girgiza kai bata ce komai ba ta juya ta shiga neman hijab har jikinta rawa yake Ya girgiza kai yana murmuahi ya fice Hijab ta dauko fari kar mai hanaye ta saka ta kara turare ta dauko takalma masu dan tudu farare kar ta saka, ta shafa lips ta juya da dan sauri domin du ji take zai fasa ne Tana fita ta ga Hafsat sai cika take an ce ba da ita za.a tafi ba Ai rauda bata iya tsayuwa rarashinta ba dan zumudi ta bi bayansa da sauri Tana fita ta ga galeliyar mota mai wani irin tsari tamkar kifi domin gabanta ya mike kamar gaban jirgi A hankali ta taka ta karasa ta ga Humaira zaune a gidan gaba ta sha itama shiri aman itama hijab ne a jikinta ta zagaya a hankali ta bude bayan ta shiga ba tare da ta yiwa kowa magana ba Cikin nutsuwa yake tuki har suka karaso gidan su Humaira Nan ta fara fita kafin Sudais ya umarci Rauda da ta fito su shiga su gaisar da iyayen Humaira Sai da gaban Rauda ya fadi, a ranta ta ayanna lalai dole Humaira ta ringa daga kai ashe iyayenta masu kudi ne haka, tap tama yi kokari domin da wata ce abin sai ya fi haka ( baki san garin ba ) Har kasa ta duka ta gaisar da mahaifiyar Humaira , ga mamakinta raji raji tamkar ba ita ce maman Humairar ba domin sam halaya bai zo daya ba Harda yar nasiha ta yi mata kan su zauna lafiya Allah ya hada kawunan su A haka sukai mata salama suka fice Tafe yake a hankali yana tuki da kansa , yakan dan waigo ya kali Rauda da jikinta du ya yi la.asar bai san dalili ba.............. Sajidar mama😍 *❣IDAN KA RAINA INDA KAKE❣* Na: *SAJIDA* *_LITATAFAN MARUBUCIYAR_* *_Duk Karyar kada_* *_Yar Mahaukaciya_* *_Neman na kaina_* *_Bani da zabi_* *_Daga tafiya daukar soja_* *_Idan ka raina inda make_* *🌈KAINUWA WRITERS✍🏼 ASSOCIATION*🤝🏻 ```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}``` https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation 4⃣9⃣ Kyauta gare ki kausar tun daga saudiya, A haka ya karaso anguwarsu , nan ta dago ta shiga bin layinsu da kallo, yana nan yanda yake ..., canjin da aka samu sai karin kwatoci da kananun yara suna yawo ko.ina datin jikinsu ma ya ishe su, Sai gugun gugun samari ana zaune ana tadi sai dan tsirarkun yan mata wasu daga makarantar islamiya , wasu an aike su, wasun kuwa kawai yawon anguwa ne basa nan basa can Daidai kofar gidansu ya ja ya tsaya Sai a wannan lokacin gabanta ya fadi, tuno auntynta da ta yi ya boye mamakin ya aka yi ya san gidabsu kwata kwata Ko mu juya? Ta ji muryarsa mai tsada ya aiko mata da tambayar Cikin nutsuwa ta girgiza masa kai Ta ce" mu mu tafi tare? Domin a yau ji take tamkar bakuwa a gidan su, sannan bata san me zata tarar ba... auntynta na nan? Me ta fadawa mamansu kan mijin da ke aurenta? Shin ya mama ta dauki lamarin? Bata ma san ya fita a motar ba sai da ya bude gefen da take ya mika mata hannunsa na dama bai iya ce mata komai ba A hankali ta saka nata hannun ta fito cikin nutsuwa aman kafafuwanta suna mata rawa Gannin mutane ta shiga kiciniyar karbe hannunta aman yaki saki Kasa kasa ya ce" *MATA* ki bani nutsuwa mana kar ki fadi Ajiyar zuciya ta saki kafin take jin dan karfi karfi ta kama kanta du da haka ta dan labe a bayansa tana bin yan anguwa da aka fara taruwa ana " lah Rauda ce, wly Rauda ce Shiga ya fara yi da salama, domin shakuwa ta shiga sosai tsakaninsa da su aba har an janye masa iyaka da gidan Mama ce ta dago tana faman hasa wuta a bakin murhu dan dora koko ta damawa Aba ya sha kafin ya fita domin yau shi kawai aka samu Amsawa ta yi tana murmushi ta mike tana kara gyara hijabinta baki har kasa sai dai me Raudanta ta hango a bayansa Du kawaicin mama sai da ta ce" Rauda? Da mamakin anya kuwan Raudan ne? Ai Rauda tamkar jira take da gudu ta je ta fada jikin mama ta saki wani irin kuka Mama kanta idannuwanta ta lumshe ta hana hawayenta zubowa, a hankali ta shiga dan bubuga bayan Rauda kafin ta dake ta cireta a jikinta ta ce" ke bana son sakarci kukan fa? Ke har yanzu ba zaki girma ba? Rauda ta tsaya tana kikifta ido tana faman komawa jikin Maman Muryar Abanta ta ji ya ce" Raudana ne? Ai da qani irin ribos ta juyo ta gansa ya fito daga daki da rigarsa doguwa jalabiya da hula , ta tabata da kayan aiki a kasan wa.innan Da sauri ta karasa wajensa ta kamo hannunsa ta dora kanta shima ta fashe masa da kuka Aba ya ce" kai kai kai, autan Abanta kuka kuma? Kar ki ce min na murna ne domin na fi so a dara min idan har farin cikin ganina ake Ai sai ta dago kai tana kallon sa ta shiga dariya hadi da kuka tana shesheka Shima ya yi dariya yana goge mata ido daidai nan ya ja hannunta wajen tabarmar da mama ta shinfida har Sudais ya yiwa kansa masauki yana kallon yanda Rauda ke zuba shagwaba Amsa gaisuwar sudais ya yi a mutunce kafin yake cewa" ka yi hakuri fa yau mutuniyar yan rigimar a kai suke an shigo da kuka Bakinta ta turo ta kara lafewa a jikin Aba tana mamakin kennan sun san wa suka aura mata ko me? Nan ma ya dan jima kafin yake tashi ya ce zai je wajen aiki idan ya taso zai dawo ya dauke ta, Da ido yake kallonta ko zata taso ta yi masa rakiya ya hana ta kukan nan aman ina sai ma ta sauka ta zauna sosai jikin mama tamkar ta koma cikinta ta ki gane yaren sa Haka ya fita yana tunanin bata ci komai ba ya fito da ita da kuma koke koken nan shi fa tana faman caza masa kwakwaluwa da tunani A hankali ta dago daga jikin mama, ta shiga waiwaigawa bata ga aunty ba, ko ta je makaranta? A hankali ta kallo mama da itama ita kawai take kallo tana jin farin cikin Raudanta ta samu konciyar hankali, Murya a shake Rauda ta ce" Mama, wai dama kun san wa kuka aura min? Mama ta ce" da farko ban sani ba, sai daga baya Rauda ta gyada kanta, ta ce" mama, ban sani ba mama, ban taba sannin shi bane sai da na gansa, na yi kuka na yi kuka har na gode Allah mama, ba zan taba amincewa da haka ba da da sani na Mama ta hada rai ta ce" me kike nufi da hakan? Rauda ta shagwabe fuska ta ce" mama baki gane shi ba ne? Shi ne fa na wajen Aunty? Mama auntyna tana fushi da ni na tabata Mama ta ce" ehe sai aka yi yaya? Rauda ta shige share hawayen idannuwanta ta ce" ba sai ya sawake min ba ya aureta? Mama ta zaro ido ta buge leben Rauda ta ce" kul, Rauda baki da hankali? Aure ya kusan kwana arba.in ki zo min da maganar mijinki ya sake ki ya auri yayar ki? Wani zama ne kike a gidanki da mijin ki? Ke ina islamiyar da kika kwashe rayuwarki kina zuwa? Me ake koya maku ne a can? Ya Rab Rauda bayan shirmen harda rashin hankali ke damun ki? Sosai mama ke fada kafin ta sasauta muryarta cikin nutsuwa ta ce" Rauda, auren shi ake kira da ba wanda ya isa ya hana shi, tabas da zai zo da wani ja.in jar mu da kafin a daura shi Allah zai sanar mana, ke yanzu kike gannin a wannan lamari kina da ja ne? Ni auren nan bani da abin fadi sai adu.a Allah ya sanya alkhairi Rauda, auren nan ina ji a jikina du wanda ya ce zai ja da shi yana cikin rigimar rayuwa, Rauda ki kontar da hankalin ki, wannan mutumin Allah ne ya hada auren nan naki da shi, ki bi shi ki yi masa biyaya a matsayinsa na mijin ki, ki faranta masa ki nemi lahirar ki, ba wanda ya isa ya ja da abinda Allah ya tsara Rauda, ki kadara in dai har auren nan naku ya rabu da wannan bawan Allah to fa Allah ne ya yi zaman ku ba mai dorewa bane, kar ki yarda ki furta masa kalmar ya sake ki koda kin furta ki nemi gafararsa, ba inai maki wannan nasiha dan yana wani a nigeria ba, inai maki ita ne dan ina son ki shiga inuwar aure ki samu albarkarsa gobe kiyama ki samu rabauta Rauda kam du ta yi sanyi, bata taba kawowa mama zata yi mata nasiha kan auren nan ba, kanta a kasa tana jin du abinda mama ke fada har ta tsaya tana sauke ajiyar zuciya domin har zuwa lokacin a hasale take da irin furucin Rauda wai ya sake ta, tana jin kunyar kanta domin tabas wannan na cikin dabi.arta , ba komai ban3 a wajenta ta yi tsaye daga wani abin ya hado su da malan ta ce masa ya sake ta a gaban yayanta ko shi ya sa du irin ilimin da ta baiwa yayanta na islamiya da boko hakan bai yiwa Rauda nauyi a bakinta ba ta fade shi gatsal haka? Hawaye ta ji sun tarun mata a idannuwanta kafin ta goge har sun samu damar zubowa Hankalin Rauda ne ya tashi ta riko hannun mama ta ce" mama kuka? Mamana kuka kike? Ki yi hakuri mama ba zan kara ba, ba zan kuma ce masa ya sake ni ba koda yankan naman jikina yake, bana son bacin ranki mama Mama ta janyota sosai kusa da ita ta ce" wai ke din mai dama daman kennan ina ga yar uwarki? Na cuci kaina na zuba rayuwa tamkar ta dabobi ina baranci a gaban yayana gashi yanzu ina gannin abubuwan da sukan iya tsayar da bugun zuciyata , Ina aikin me na ringa ginawa kaina ramin mugunta ina muzantawa mijina a gaban yayana a tunanina isa ce dan na isa da shi ni yar wane ni yar gata ni meron miji ina tuka sitiyarin ragamar rayuwarsa ina iza shi du a tunanina isa ce ashe ni na gama ginawa kaina ramin da in ba Allah ya tsaya min ba idan na afka na kade ? Mama ki daina irin magangannun nan , ba zan kara ba na yi maki alkawari ... Rauda ta kuma fada tana kara rike mamanta Mama ta ce" ba zaki fahimta ba Rauda, Aman yanzu ki misalta min irin yanda hankalinki yake tashi idan ina hawaye? Rauda ta shiga kikifta ido itama tana hawayen a hankali ta ce" ya fi karfin kwatance hawayen mahaifiyata Mama ta lumshe ido ta ce" ki taya ni kara rokon gafarar abanku, ya yafe min aman ya kara yafe min ya saka min albarka, Rauda du irin girman darajar miji da Allah ya ce *Da zai umarci mutun ya yiwa mutun sujada da ya umarci mace ta yiwa mijinta sujada* , aman na take, na halbe, na dane, na yi ta wasa da shi tamkar birin wasa na, Sai dai na godewa Allah da ya nusar da ni kafin na koma gare shi a irin wannan rayuwa Tashin hankalina a yanzu shi ne ku yayana ... bare ke da Allah ya nuna min kin yi auren Rauda shin a ya kike daukan girman darajar wannan sunna wato *MIJI?* kina da niyar aiki ko nace kamanta yanda ma.aiki ya koyar da mu dan gannin kin kare hakokin *MIJIN KI?* Mama ki dakata mama, dan Allah mama ki daina tsoratar da ni! Rauda ta fada tana mai rusa kuka Mama ta ce" kina tsorata a yau a gabana dan na titsiye ki, ni mahaifiyar ki ina da ranar gobe kiyama idan Allah ya tsayar da ke da litafin rayuwarki ya hasko ki gaban bainar nasi ya kirayi sunan ki ya bayanar da fila fila a aikace aikin da kika aikata a gidan duniya tunva na mijin ki ba ( la haula wala kuwata illa bilah,,,, 😭,,,, ya Allah ka bamu ikon kamantawa, ka bamu ikon yina mazajen mu biyaya mudin ran mu ) Da sauri Rauda ta fada jikib mama ta rungumeta, tana hawaye a hankali har ta samu ta dan tsagaita jin mama ta yi shiru tana taping bayanta dan ta yi shirun itama Murya a raunane ta ce" mama, tabas dan adam butulu ne, yakan mance duban alkhairin da Allah ya babaye shi da shi rudin duniya ya rude shi, Wani lokacin tsoro da fargaba da nagatan da basu tsoron Allah kan kai bawa ga aikata laifi mafi muni ga wanda ya yi duniyar da abubuwan cikinta baki daya..... mama ina zamu je? Ya zamu yi? Me muka tanada? Me zamu ce masa? A hankali mama ta ce" *mu gyara, sai mu samu rabauta domin shi din gafurun rahim ne Raudana* Mama ta ci gaba" du wace ta ce maki kalau ne, ita mijinta bai taba yin fushi da ita ba, ko bai taba daga mata murya ba, ko ya kasance yan rigingimu na yau da gobe tace ita bata sani ba karya take, ta fada maki haka ne dan gadara da karya sai dai kuwa idan ba a hayacinsa yake ba wato asiri wanda na rantse idan har kika yarda kika yi shi ko a kiyama kar allah ya hada ni da ke Rauda, biyayar nan dai, hakurin nan shi na toke ki da ki yi kar ki yi anfani da abinda na aikata a baya ki yi kokarin gyara naki kema rayuwar idan ransa ya bace ki yi shiru, idan naki ya baci ki tausashi zuciyar ki kar ranki ya bace ki ringa sakin magangannun da ba da.a a ciki Kanta kawai take gyadawa bata kuma cewa komai ba Aba ya saki murmushi, ya juya a hankali ya koma dan samo masu koda kosai ne su ci domin kuwa coco sai dai na gobe in da rai, Yana alfahari da Mariamarsa, yana jin wani irin kuzari har daga kai yake shima ya fito magidanci, matarsa na shayin bata mata domin *Indalahi* Sai wajen karfe biyar na yama Sudais ya yi salama, Rauda dake tuka tuwo ta mike tana amsawa kafin ta rage idacen murhun dan kar ya kone ta tako a hankali jikinta du a mace haka ta wuni domin mama batai kasa da gwuiwa ba wuni ta yi tana kara kusantata da ni.imar aure harda yan dabaru da karin jadadawar hakuri shi zai sa ta ci riba Kallonsa take tamkar ta ga sabuwar halita, a hankali tamkar gidansu ya karasa ya dauko hijabinta ya saka mata, cikin nutsuwa ya kamo hannunta ya ce" *Mata* shiga daga ciki ina zuwa Juyawa ta yi ta shige ciki bisa umarninsa , shi kuwa ya yiwa samir bip suka shiga shigowa da abinda ya zo da shi dan cin yau kawai More cmment more pg😉 *❣IDAN KA RAINA INDA KAKE❣* Na: *SAJIDA* *_LITATAFAN MARUBUCIYAR_* *_Duk Karyar kada_* *_Yar Mahaukaciya_* *_Neman na kaina_* *_Bani da zabi_* *_Daga tafiya daukar soja_* *_Idan ka raina inda make_* *🌈KAINUWA WRITERS✍🏼 ASSOCIATION*🤝🏻 ```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}``` https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation 5⃣0⃣ Page din ki ne *MADAME DAKKWARO* 💓💓💓💓💓💓💓💓💓💓💓💓💓💓💓💓💓💓💓 ( *Walahi na tsani sticker, idan kina da damar yi min comment ki yi min plz idan kuwa ba dama ba laifi aman kar ki yi yunkurin sakoni a gaba da na yi typing😉* ) Kallon kayan kawai mama take, kayan abinci ne na cikin carton carton, ga su jus da chocolate Ita kanta Rauda zuciyarta ta cika da murnar hakan duda ta san hakan ba komai bane a wajensa aman kam tana tare da farin cikin yau mama da aba zasu more da kayan marmari Haba haba kai kuwa, kayan nan mu je ina da su? Gashi irin na sakawa a frij ne idan ba.a saka ba suna iya lalacewa? Aa ko malan ya dawo ya tarar da abin nan kuma na karba zai saba min ne aa ya dawo su kwashe ka yi hakuri Mama ta fada tana ta mamakin wannan abin Sudais ya ji wani abu ya darsun masa a zuciyarsa na kaunar datijuwar wato mahaifiyar abin kaunar sa, aa wai ita ce ko me ya sameta? Lumshe idannuwansa ya yi bayan lura da ya yi Raufa sai sakin murmushi take , ya ce" mama daman d'a na yiwa iyayensa alkhairi su maido? Ko dai ni din ne ba.a haihuwar da ni? Ya karashe yana shagwabe fuskarsa sosai irin na yara kannanuwan nan Kunya ce ta kama mama, Rauda kuwa ta zaro ido tana kallon sa ta ce" lah Sire menene haka wai kamar wani baby? Mama ta zaro ido ta kallota ta ce" ke? Ya ishe ki haka bar shi ya yi bacinsa ai mamansa ya yiwa, Murmushi ya saki kafin yake yo mata gwalo ita kuwa ta yi gagawar rufe idannuwanta da hannunta tana murmushi wai ta ji kunya Maama ta yi murmushi kawai ta kawar da kanta, ita soma take ta gudu domin ta lura mijin Rauda ba ya jin kunyar yin wani abin Suna haka Aba ya dawo kafin suke mikewa dan tafiya Aba kansa fadan yawan kayan ya yi ya ce sam baya son irin haka ya je ya rike masa yarsa da kirki kadai ya isa ya saka shi farin ciki har karshen rayuwarsa , sannan ya shiga yi masu nasiha kan zaman tare da hakuri ya dora da cewa" idan rai ya baci hankali ke nemo shi, sannan ya zama wajibi ku sani zaman tare na dorewa ne idan ana tataunawa , koda wani abin ya faru tsakanin ku ku yi kokarin gannin kun tatauna a tsakanin ku da yardar Allah zaku samu hanyar samun lumana a tsakannin ku Sosai Sudais ya ringa jin wata nutsuwa tare da sirikan nansa harma ya dora ayar tambaya a irin kallon da ya yiwa mama da farko (shiryuwa ta yi Sudais) Shagwagwabe fuska Rauda ta yi kafin take fashewa da kuka tana kallon iyayen nata, tafiya zata kuma yi ta bar su? Kai ina iyaye dadi ne da su komai dadin da kake ciki nesa da su ragage ne (annata😟😟😟😟😭) Sai da Aba ya yi rarashi kafin take yin shiru mama kuwa hararta kawai take kafin ta girgiza kai, kai Rauda ba wayo Har sun kama hanya ta dawo murya a raunane gannin har dare ya yi ta ce" mama, Aba wai ina aunty ne? Na yi tunanin ko tana makaranta gashi kuma har yama na yi bata shigo ba? Ko har dare suke kaiwa? Mama ta kalli Aba , Aba ya kale ta , ta kikifta ido ta ce" ke, ki je mana yana jiran ki zaki dauko wani zance kuma? Rauda ta yi tsaye tana kallon su, du sun dan daburce ba kamar mama da ta shiga sosa hannunta na hagu tana dan zaro ido , takan yi haka idan ta daburcewa wani abin Matso su Rauda ta yi da kyau ta ce" me ke faruwa? Mama ta ce" ba nace ki tafi ba? Malan ya mika hannunsa ya kamo na Rauda ya ja ta wajen kofa, daidai soro suka tsaya ya kaleta da kyau ya ce" ta zabi tafiya ta bar mahaifanta kan dalilinta, ta yi mumunan fushi da mu ta bar mu Cike da tashin hankali Rauda ta ce" Aba, ta bar ku? Ta je ina? Aba ya sada kansa ransa na suya, ya dago ya kali sama ya ce" ta shiga Duniya bayan ta fada mana cewar ta barmu ne zata je ta samawa kanta farin ciki Tashin hankalinta ya karu ta ce" Abana, dalilin an aura min wannan bawan Allah aunty har abin nata ya girmama ta fita daga gidan nan? Ina zata je ? Wajen wa? Wanene yake tare da mu da zuciya daya sama da iyayen mu? Meke damun aunty? Aba ya ce" rudin shaidan da son zuciya, sannan ko daya ba dalilinki bane, son abin duniya ne ya rufe mata ido, ni ba zan yi mata baku ba ko kadan sai dai adu.ar Allah ya takaita mata wahalar da zata gani a duniya Rauda da ta fara hawaye mai yawa ta daga kanta tana kallon sararin samaniya , can ta ce" ta yi mata girma, fadinta da abinda ke cikinta sun fi karfin tunaninta, a bar aunty a iya anguwarnan ma ta fi karfinta bale duniya Abana, ya Allah ka shiryar mana ita, ka shirye mu baki daya , Abannna ku yi mata adu.a in sha Allah zan tambaye shi da izinninsa zan gwada nemanta Rauda, ki je kawai, zata dawo.....ina mai tabatar maki wajen nan da take yiwa kallon kurkuku sai ya zame mata wajen mangarinta, adu.a kam munai mata sosai fa Haka Rauda ta fito jiki a sanyaye ta nufi mota sai dai yanzu baya ta shiga domin Samir ne ke jan su Haka suka biya gidan su Humaira sai dai mamanta ta ce ta tafi Suna zuwa gida Rauda ta bude dan shigewa cikin gida Bude gefensa ya yi ya kamo hannunta na hagu dake kusa da shi Samir na gannin hakan ya fice ya yi nisa da su A hankali ta dawo ta koma cikin motar ta sada kanta domin ta san magana yake son yi da ita A hankali ya fito ya dawo bayan shima ya shiga ya rufe motar Shiru kake ji , ita bata dago ba shi kuwa bai yi magana ba ya tsareta da kallo Jin shirun ya yi yawa ya saka ta dago da kanta ta kai dubanta wajensa , da sauri ta kawar da idannuwanta tana kokarin mayar da kallonta wani gefe Idan har kika bari hawayen idannuwanki suka kuma sauka kan fuskarki na yi maki alkawarin hukunci mata Da sauri ta shiga ajiyar zuciya tana hadiye kukanta bata yarda hawayen sun fito ba dan bata san irin hukuncin da zai yi mata ba Menene? Sudais ya jefo mata tambaya hankalinsa konce tamkar ba abinda ke damunsa Tana ajiyar zuciyar ta kallo shi, ta ce" ba.....ba komai Mama kike so? Ya kuma tambayarta tamkar kana tambayar yaro dan jaririn da baya fahimtar yaren ka Kai ta kara girgiza masa tana hadiye kukanta A hankali ya furta" ya Allah Hannunsa ya kai daidai kirjinsa wajen zuciyarsa tana kallonsa kamar yanda yake kallonta, murya a kasa sosai ya ce" ki daina yawan kuka kin ji? Ki sama min natsuwa Ita kam takan yi mamakinsa idan yana furta ta sama masa natsuwa, wace irin natsuwa kuma? Kukan nata na hana shi natsuwa ko me? Sai dai bata iya bashi amsa ba ta gyada masa kai kawai ta shiga kokarin fita a motar domin bata da bukatar da ta fi ta je ta yi wanka ta yi alwallah ta yi ta sallah ta yi ta adu.a ko ta samu sauki, ita kam ta cika rauni du ji take wani iri Hannunsa dake cike da gashi baki sidik ya miko ya kamo nata da kyau ya rike, ya jima a haka kafin ya ce" Freind? Kallo shi ta yi, Freind kuma? Da wa? Mijin nata ne ke tambayarta zama abokinta? Shi kam yana zo mata da abubuwan mamaki Eoooooo? Sudais ya furta yana farkar da ita daga tunanin da ta afka Kallo shi ta yi kafin take bin hannayen su da kallo, hannunta sai ya zama wani dan firit a cikin nasa, shi kam komansa haka ne gabjeje? Kin aminta na zama Freind din ki? Irin mu zama abokai na ku da kut.....kina fada min damuwar ki farin cikin ki...da sauran su ... nima haka? Da mamaki ta saki baki tana kallon sa ta ce" kuma mace da namiji abota? Kuma ma kai katoto ne.......😳 shiru ta yi kafin ta kai hannunta ta rufe bakinta da shi Ido ya zaro ya ce" kai kai kai, ni ne tulelen? Gabjejen? Dankareren? Ta yi saurin bude idonta ta ce" kai kai kai aa ba haka nace ba sire Ya yi murmushi ya ce" kin ga ni ne sirin ki, abota idan na yi da ke bai haramta ba, ina son zama abokin ki ne dan rayuwa ya kasance muna taimakekeniyar juna Rauda ta tsare shi da kallon da bata san ta yi masa ba, sajensa, lebensa, girarsa, dara daran idannuwansa, sai ma idan yana shagwaba tambar karami, murmushi ta sakar masa ta kai dan yatsanta ta ce" mu kula Shima murmushin ya yi gannin ta dan saki ranta ya mika mata suka kulla kafin yake yi mata salama ta fice tana waiwayensa tana yi masa bye tana murmushi Samir ne ya dawo yana dariya kasa kasa ya shiga ya tada mota Juyowa ya yi ya tsare sudais da kallo kafi ya ce" sai ina oga? Ya fada yana sakin murmushi mai sauti Sudais ya hade rai ya ce" kai dariyar me kake? Samir ya shiga tatayinsa ya ce" ba komai Sudais ya ce' mu je zoo Ke kina da hankali kuwa? Me ke damun kwakwaluwar ki? Mariama tarbiyar da ta baki kennan? Kazar nan guda daya ce sukutum ke daya na bari a falon nan daga na shiga wanka na fito na tarar kin cire fifike guda ki wani ce ba ke bace? Dan ubanki abincin elhaji ne idan ya dawo ya kike so mu kare da shi? Ohke bakin ciki kike yi min ina zaune a gidan daula ina bin mijina ba kamar uwarki da ta raina mijinta ba? Kin taba gannin na dagawa mijina murya? Ko dai so kike ya sake ni ya aure ki ne? Aunty ta karasa tana daga muryarta sosai Innalilahi wa.ina ilaihi raj.une, Aisha ta fada tana dafe gefen fuskarta da aunty ta yayarfa mata mari , ta kallo wajen Sarah ta ce" Sarah ki fada mata, wly ban dauka ba, bani bace , ni da a nan na bar ku na shiga dan yin sallah? Sarah ta dago daga danna wayar da take ta ce" ah mu kika bari? Kina nufin ni na dauka dan uwarki da ubanki mai datin hula? Sarah ta fada tana tasowa a mugun harzuke ta nufo Aisha Hannun da ta ci naman da shi ta manta ta dago dan kaiwa Aisha duka Aunty ce ta gani ta dan zaro ido, bata kuma cewa komai ba kawai ta juya dan barin wajen ta je ta sake masa wata kazar dan kuwa ta sani ne idab ya ga kazar nan a haka ko wa yayi mata tsaye sai ya ci mata mutunci ya tsigeta sama da kasa ya tsinewa iyayenta Da Sauri Aisha t kauce ta ce" ke kar ki sake kin ji? An fada maki ni ganga ce? Sarah ta yi murmushin yan duniya ta ce" aa, ganga fa mai kawo kudi? Ke ai jaka ce mai cinye abincin mutane banza sakara Aisha ta ce""""" *❣IDAN KA RAINA INDA KAKE❣* Na: *SAJIDA* *_LITATAFAN MARUBUCIYAR_* *_Duk Karyar kada_* *_Yar Mahaukaciya_* *_Neman na kaina_* *_Bani da zabi_* *_Daga tafiya daukar soja_* *_Idan ka raina inda make_* *🌈KAINUWA WRITERS✍🏼 ASSOCIATION*🤝🏻 ```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}``` https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation 5⃣1⃣ ( *imanin dayanku ba zai tabata ba har sai ya sowa dan uwansa abinda yake sowa kansa........* ) Aisha ta ce" ni ce jaka sarah??? Sarah ta yi mata kallon tsaf ta ja tsaki ta ce" jakinma ya fi ki daraja.....kafin take juyawa tana ta kokarin juya yan shafafun duwawunta Nan ta bar Aisha ta zauna ta daga kanta sama, rabonta da ta gane kan mutanen nan tunda ta zo zama cikinsu, wai wani mumunan hali ne da ita da ya sa suke yi mata haka ko me? Aman ai ita yar uwarsu ce ko ba komai ance dan uwanka dan uwanka ne ya fi gaban wulakanci Wannan kennan Cike da nutsuwa kamar yanda ta saba ta gabatar da salarta , ta jima saman salaya tana adu.a , bata kai ga shafawa ba ta ga ya shigo, direct wajen salayar ya nufo hannunsa dauke da plat Da ido ta tsare shi har ya zauna ya yi irin zaman makaranta wato ya tankwashe kafafuwansa ya ajiye plat din a tsakiyar su wanda ta bi shi da kallo pizza ce na ciken Adu.arta ta kai ta shafa wanda ya daga hannunsa ya shafa shima, Riga ce a jikinsa mai botira sai dai botiran du a bale suke sai fara daga ciki , da wando dan dogo irin na dari ya kame daga can kasa Yar yukar ya mika mata da cokali mai yatsutsai ya yi mata nuni da ido cewar ta yanko su ci Karba ta yi ta shiga dan kokarin yankawa aman tana satar kallon sa ta ga shi hankalinsa konce sai wani dan kakauda kai yake dai Yankawa take tana mika masa yana karba , shima sai ya yanko ya miko mata Na farko karba ta yi ta kai bakinta, ta sha jin labarin pizzar nan a wajen yayan masu da shi da yan mata yan gayun ajin su , yau gata ga pizza Harda lumshe ido ta kai bakinta bayan ta yi bisimillah Dan bude idannuwanta ta fara a hankali, ta ga dai abin ba mai gyarata bane sai ta bude gaba daya Yatsina fuskarta ta shiga yi tana kallon sa, Shima ita yake kallo, a ransa yake ayyana ya haka ko dai bata son ta chiken? Kokarin hadiyewa take, da kyar ta samu ya shige cikinta ta shiga sauke ajiyar zuciya wata na korar wata Matsowa ya yi ya ce" lafiya? Me kika hadiya a ciki freind? Kallo shi ta yi, kunya take ta ce masa ba dadi domin bata san a me zai dauki hakan ba, wata zuciyar Ta ce da ita ke ya fa san wacece ke , ya ga gidan ku, ya dai san ba kudin shinkafa da dawa za.a saka a sayo maki pizza ba dan haka ba wani abin kunya a dan kin kasa ci Fuskarta ta kara yatsinawa ta ce" ba dadi Ido ya zaro ya ce" ba dadi fa? Ko kin fi son na jan nama? Rauda ta kawar da kanta ta ce" ni abin ne, wani yami yami, manda manda, ni fa ban san me ake so na ji a cikinsa ba Ido ya zaro, maimakun ta bashi dariya sai ya ji wani sanyi a ransa, bata da kiriniya ya tabata da tana da shi da ko bata ci a wajen kawaye ba zata saka saurayi ya sayo mata A hankali ya shiga fitar mata da dan nama naman wajen da ya fi naman , ya hada da dan cream din kadan ya yo wajen bakinta, Ido cikin ido ya ce" ha Idannuwanta ta shiga kikiftawa ta ki bude bakin domin itafa bata ji dadin abin ba , kai yan gayu suna bata mamaki wani lokacin su kansu suna cin abin ne kawai dan dai su nuna sun isa ko dan vitamine ko meye ma su damiwarsu wai Make kafadarta ta yi tana turo bakinta Murmushi ya yi mata har hakoransa suka bayana ya ce" kin ga, ki yarda da ni, ki taba wannan idan ba dadi sai a hakura Yawu ta hadiye ta bude bakinta da kyar, ya samu ya saka mata yana kallon ta, Dan taunawa ta fara, nan ta ji wannan din kuma da dan dadi ba kamar inda ta cira dazu bane, sai dai kanshin nan dai nasa ne ita kuwa bai wani yi mata ba, Da kyar dai suka gama cin abincin ya fitar da game a wayarsa ya saka masu lido suka koma bakin bed suka shiga bugawa Nan fa gardama ke sarkewa har Rauda ta fada kansa tana titirjewa ita bata yarda ba yana mayar da ita gida da gangan a sake A haka dai suka zauna har dare ya yi sosai wajen karfe biyu suna shirme basu ankara na sai da ta fara jin idannuwanta sun yi mata nauyi ta kalli agogon dakin nata Ido ta zaro ta kallo shi ta nuna masa Shi kansa ya yi mamaki, to ya aka yi lokaci ya yo gudu haka ? Fuska ya shagwabe ya ce" to ki raka ni, ni tsoro nake ji Rauda ta zaro ido ta bi shi da kallo ta kalli kanta, bata san lokacin da ta saki dariya mai dan sauti kadan ba, rana yi tana nuna kanta kafin kuma ta nuna shi Shima dariyar ya yi ya ce" kin ga ki daina gannin girman nan nawa bani da nauyi fa, zo ki ga ki goya ni Rauda ta kara yin dariya ta ce" idan na goya ka, ina mai tabatar maka na tashi a aiki, tap rabewa zan gida biyu Shi kam dariyar nata ke burge shi, baya jim zai iya fita ya barta a haka sai dai baya so ta kawo wani abin cikin ranta dan haka ya mike ya dafa kanta ya yi mata adu.a tamkar baby ya shafa mata a hankali yana kallon kwayan idannuwanta ya karasa har saman goshinta ya yi mata kiss da lebensa ya sakar mata muah ya dan shafa gashin kanta ya cafke hannunsa da nata ya ce" ki huta *MATA* hannunta ta daga masa a hankali itama tanai masa bye, sai dai sam bata so ya fita a wannan tsohon daren duda ta san was yake mata sai dai ta mike a hankali bayan ya dan jima da fita ta bi baya dan gannin ya tafi? Sai dai ba fita zata yi ba bakinta daga nan bakin kofarta Sudais na fitowa ya ga Humaira zaune saman kujera ta dafe kanta da hannayent bibiyu A hankali ya karasa wajenta ya tabata ya ce" Humaira lafiya? Me kike har yanzu a waje? Dago da kanta ta yi da idannuwanta da suka canja launi ta sauke saman kansa, , ranta bace ta ce" dakinta? Me kake a dakinta har wannan lokacin? Samir ya zo yayi ta jira baka fito ba, ka bar wayoyinka a dakin ka, sannan da ka shiga ka saka kofar a blinder yanda ba zaku ji mai kiranku ba koda bugawa za.a yi? Wannan wani irin cin fuska ne da cin zalin? Ka gama da ganga zaka yar da ita ne? Na zama kaya ne har zaka zubar da ni a kondon shara? Me na yi maka haka? Ta karashe tana fashewa da kuka, ta ci gaba da fadin" baka taba fin minti ashirin a dakina ba, baka taba taraya da ni a dakina ba, aman ka duba ka ga A hankali Sudais ya kai hannunsa zai tabata domin a gaskiya takan bashi tausayi wani lokacin, Humaira ta cika daukan abu da zafi, kiahinta ya yi yawa, haka fa da ran Khalisat har tambayarta take wai idan yana saduwa da itae yake cewa ko irama yakan yi mata shiru ne tamkar gunki? Ita ta ji ana cewa maza ihu suke harda kuka aman kawai Sudais sai dai ya wani yi mata shiru ga shegen nacin.....abin nan🤣 Da sauri ta ja ta ce" kar ka taba ni, kar ka taba ni ni, baka yi wanka ba , ka je ka wanke datin da ta kwaso, karamar yarinya har ka iya tausheta haka? Ni kar ka taba ni ka koma kawai ka waye a dakin nata Cike da takaici Sudais ya ce" ke ki daina yi min magangannun shirme mana, idan ma hakan ne ba matata bace? Ko kin taba jin an ce na dane wasa ba tawan ba? Bare ma ni ba abinda ya shiga tsakanina da ita, wannan karamar yarinyar zan jewa? Ba sai na halakata ba? Ke kanki kin san irin matan da nake iya zuwar ma, dan haka kar ki yarda ki caja min kwakwaluwa rainon matata nake Da sauri Rauda ta koma ta rufe dakin ta nufi tsakar dakinta Kai kawo ta shiga yi, "wannan yarinyar zan jewa? "Ba abinda ya shiga tsakanina da ita "Ke kin san irin matan da nake zuwarma Kishiyata yake fadawa ba abinda ya shiga tsakanina da shi? Ya Allah, me hakan? Rainona yake? I.m 22 old, aman ya kiraye ni da wannan yarinyar? Shi din menen girman nan nasa? Anya kuwa ? Ni ba mahaukaciya bace koda ban je university gidan kowa ba na je islamiya, Ohk shi nan sai na girma kennan zai san matarsa nake? Shi ya sa ya kula kawance da ni? *zan gani sire ni da kai wa za.a rainan* A yau Aisha ta yi shirin komawa yar uwarta bayan ta yi bincike ta gane gidanta, Sannan sarah ta sauko harda ara mata kaya dan su je tare domin aunty ta kashe kudi sosai dan karkata hankalin Sudqis daga Rauda ya saketa ya tsaneta ya karkato kan Sarah ko sa samu damar wanke goma su tsoma biyar *BAK'A CE* *❣IDAN KA RAINA INDA KAKE❣* Na: *SAJIDA* *_LITATAFAN MARUBUCIYAR_* *_Duk Karyar kada_* *_Yar Mahaukaciya_* *_Neman na kaina_* *_Bani da zabi_* *_Daga tafiya daukar soja_* *_Idan ka raina inda make_* *🌈KAINUWA WRITERS✍🏼 ASSOCIATION*🤝🏻 ```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}``` https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation 5⃣2⃣ *BAK'A CE*........... NA NAN TAFE I.A Tana shiryawa da daridari ne, dan kuwa ko a jiyan da dare sai da suka tsigeta bayan nan ne ta shaidawa aunty ta samo gidan Rauda tana son zuwa gobe da yama abinka da marar kunya a nan suka shiga nuna mata soyaya Har nan nema sarah ta fauko mata wata rigar atampa da ta sha mahaukacin dinkin zamani ta bata cewar ta saka wannan dan kar su je a hana masu shiga Bayan ta gama shiryawa Sarah ma ta gama hadewa cikin wani material dan ubansu tana ta kallon Aisha, a gaskiya Aisha ta hadu ... haka take ayannawa a kasan zuciyarta sai dai kuma banza ce sam ba yar gayu bace yanzu zaka nuna mata ta yi maka ta kawo maka hauka Haka suka fito Aunty ta ba sarah wani turare a kwalba ta yi mata signe da ido Har sun fita Sarah ta ce tana zuwa ta yi mantuwa ta koma wajen Aunty Aunty ta ce" kin ga turaren nan? Ki tabatar ya shaki kanshinsa idan kika fesa, kar ki fesan ma sai yana wajen, ku like mata ki tabatar kin bugo mana shi fa Sarah kin ga uban gidan abanki ne yau ya kasance ya zo gidan nan neman auren ki hango min ci da cinyewa .... shikenan mun haye Sarah ta saki murmushi ta ce" karki damu mom zaki samu abinda kike so Ta cusa kwalbar a cikin breziyarta ta fito ta shiga motar ta tayar suka harba bakin titi A yau Rauda ta farka da damuwa domin kuwa tsaf ta kwana tana tunanin irin abinnan da Sudais ya yi,, ya zai cewa kishiyarta wai wani yarinya ce ita ba abinda ya shiga tsakaninsa da ita? A hankali ta mike ta je wajen Hafsat, bayan sun gaisa ta ce" sister kina da data ne? Hafsat ta yi murmushi ta ce" hajiata Wifi ne ai a gidan naki baki ga sai shanawa nake ina hawa kyauta ba? Murmushi Rauda ta yi ta zauna gefen bed din kadan ta ce" ina son dogon aiki da dayar wayarki, ina iya aronta wunin yau? Hafsat ta mike tana dariya ta ce" ban san ya aka yi har yanzu oga bai baki waya ba, aman na san da dalilinsa, gata ki je har adadin da kike so danma kin fi karfin rike irinta da na baki kyauta Rauda ta dan jujuya katuwar wayar kirar samsung s8 ta yi murmushi, bata ce komai ba Kunawa ta yi ta shiga cikin uc browser, ta rasa ina zata shiga dan haka ta koma ta zauna ta ce" na ji aunty na fadin a cikin nan akan iya samun ap na komai ko? Hafsat ta karba ta zauna sosai ta ce" kin ga, idan kina son shiga wajen harkar vidios, ko wace iri ce hausa turanci yare daban daban, sannan ko me kike son gani a ciki ki shiga youtube, idan kuwa ap kike so a nan saman wajen zaki rubuta sunansa zai baki Haka dai ta nununawa Rauda abu uwa sosai a wayar kafin take yin godiya ta mike ta fita ta nufi dakinta tana turo baki a ranta ta ayanna gabjeje du kibar nan sai ya kara cin karfe , ta kebe bakinta ta fada saman bed dinta Zama ta yi, ta yi shiru, ita dai bata da mutumin da zata tambaya yaya ake tarairayar miji, wannan abin kuwa dole sai an koya ba karamin abu bane..., Ta jima tana nazari kafin take sakin murmushi, Wanka ta salo, ta dawo ta saka doguwar riga marar nauyi kawai ta fesa turarukanta ta zauna ta jawo wayar ta shiga YouTube dan samun haske a abubuwan dake duhu a gareta, ta dauko vidios masu dama, wasun har rufe ido take idan tana sauraro wai kunya sai kuma ta saki murmushi ita daya Haushi haushi yake kallon su a kofar gidan a tsaye suna ta yiwa sojawan wajen magiyar su bar su su shiga Banban sojan nw ya fito fuskarsa a hade da yar karamar waya a hanunsa, Yarensa na ganinsa suka sara masa sannan sukai shiru dan sun san in dai shi ne ya fi su hauka zai yi fata data da su ne, Wa kuke nema? Wajen wa kuka zo? Ya jero masu tambayoyin fuskarsa na nuni da zaku ci ubanku ne Kallon juna suka yi, a hankali Sarah ta matsa kusa da Aisha domin sarai ta san su waye , ta san me suke iya yi, kurma suke kiransu a cikin gari domin basu da mutunci, wani bariki budurwa ba zai hana su ci ubanta ba Aisha ce ta shiga inda inda ta ce" wawa wajen Rauda muka zo Ke ba.a kama sunayen matan gidan gatsal haka! Ta san da zuwanku ne? Ya fada muryarsa na amo tamkar muryar Sudais Kifta ido ta shiga yi , sai ga wayar hannun nasa ta yi kira Dagawa ya yo ya ce" oga barka da safiya Sudais ya amsa ya yi shiru, so yayo da ya bada umarnin a yi masu lulusar fitar hayaci , sai dai wani abu yace masa ya bar su su shigo ya ga ya zata dauke su? Ya zasu kaya Murya a dake ya ce" su shigo Yana gama fada ya kashe, Sojan ya ce da su" mu je! Yana gaba yana tafe irin na kakarfan mazan nan su kuwa suna biye da shi a dan guje guje domin ba zasu iya tafiyarsa da yanga ba Gaba dayansu kansu ya daure, gidan nan a garin nan? Basu taba kawowa ransu tsaruwarsa ya kai haka ba, yanzu Rauda ce ke rayuwa a gidan nan a matsayin matar gidan? Rauda mafi kaskanci a cikinsu wace ko kwaliya bata iya ba? Ko wanka bata iya ba? Suna wannan tunanin suka karasa kofar baban falon Falo mai abin mamaki, falo mai tsari tsari mai daukan hankali Yana bude masu ya juya ya koma Sudais dake zaune ya umarci Hafsat da ta je ta kirayo Rauda, ta fada mata ko su waye kafin ta fito sannan tana fitowa ta basu waje A hankali ya daidaita camerar falon da son (kara) yanda zai iya jin me suke fada (akoyta fa sai dai tsada) Sun kusan minti ashirin a zaune, an gabatar masu da du wani dan abin motsa baki ga sanyin ac ga katuwar tv na hasko kasashen larabawa Cike da nutsuwa take takowa bayan ta riki adu.a.o.i a bakinta a matsayin makaman da zasu kareta da dukan fitinar da auntynta ta zo da ita Tana zuwa ta saki fuskarta ta yi masu salama A tare suka waigo wajenta, rigar nan ce dai ta dasu mai ruwan hoda sai ta daura dan karamin dan kwali a samn kanta ta yi dauri kawai dan rufe kai ba dan kwaliya ba, sannan rigar kananuwan hanaye ne da ita, sai wayar wajen Hafsat da ta ara ta fito da ita domin tana tsakan karanta wata ap ne na yanda mutun za yana kara kula da jikinsa da sauransu Fara.a ta bayana a fuskarta ta kara yi masu salama Sai a sannan suka farga, Aisha ta ce" eh lale Rauda, hajia kika zama shi ya sa kika shanya mu a nan ? Mun fi awa muna zaune hakama kafin a bar mu mu shigo wajen ki sai da mukai ta magiya ? Kennan ke ba zaki yi zumunci ba ko? Rauda ta yi murmushi tana mai nemawa kanta wajen zama kusa da su ta ce" lah aunty ai ban san kuna zuwa yau ba, tsarin mai gidan ne hakan Sarah ta gyada kai a ranta take ayanna zaki ci ubanki sai ganninsa ya yi maki wuya nan gaba Aisha ma ta yatsina fuska ta ce" ka ji masu gida, ke yanzu kina rayuwa a gidan nan, kin ci kin tayar da kai aman iyayenki na gidan laka? Da mariga ta yi shikenan su da gannin haske? Rauda ta sauke kanta kasa, ta dan jima kafin take dagowa tarrrrr ta ce" *ALLAH YA SAN DA ZAMAN SU* Sarah ta kama baki ta ce" kai kai kai, ke zumunci fa ya kawo mu wajen ki ba neman wani abin ba, ya zakina sakar mana magangannu haka sai kace wa.inda muka zo yaki? Waima ina mijin *namu* yake ne ya fito mu gaisa mana? Rauda ta tsaida kallonta kan Sarah, itafa yarinyar nan tunda take magana mai tsayi haks bata taba hada su ba, kai ita bata ma yarda da ita ba kwata kwata, Idan Rauda ta baiwa Sarah amsa, to lale bangon dakinma ya yi magana, share maganarta ta yi tamkar bata yi ba wanda hakan kuwa ya bakanta mata rai sosai Aisha kanta ta dan ga canji sai dai ta danganta hakan da yau yan rashin maganar ne a kan Rauda dan haka ta matsa kusanta ta kamo hannunta na dama ta ce" Lallana, Rauda ta dago ta bata hankalinta gaba daya, ta amsa da" na.am Aisha ta ce" kina tune ranar da na san Elhaj Uban Masu Gida kike aure da kina kukan nan kin ce" *Aunty kar ki yi fushi da ni, ni zan nemi ya sake ni sai ya aure ki* an yi haka ko ba.a yi ba? Rauda dake kallon ta ba ko kifta ido ta ce" Eh haka an yi Aisha ta kara matsawa sosai ta ce" na zo ne kan hakan Rauda, ke kin fi kowa sannin irin yanda nake son sa ko? Ke nake baiwa labarin idan na aurw ahi ga yanda zan tafiyar da rayuwar mu ko? Ke dai ke zaki baiwa labarin bana hada soyayarsa da na kowa Rauda da gabanta ke faduwa ta gyadawa Aisha kai ta ce" eh Aisha ta ce" ki cika min mafarkina, ki tabatar min da hakan na iya yiwuwa , na tabata tunda kika furta kalmar ya sake ki ya aurw ni ba abinda ya shiga tsakaninku, ina fatan har yanzu zaman doya da man ja kuke Rauda ta tsareta da ido, ikon Allah haka ta furta a kasan zuciyarta, Ki bani amsa mana Lallana, Aisha ta fada tana kara kallon ta Zara zaran gashin idannuwanta ta lumshe, a hankali ta bude ta ce" aunty me kike son sani takamai? Aisha ta ce" ki fada min wani abu ya shiga tsakaninku ne? Rauda ta ce" aunty ai wannan siri ne mai girma wanda idan na bayana shi Allah zai kama ni gobe kiyama, insha Allah zan rike sirin mudin raina Ido Sarah ta zaro ta ce" ta faru ta kare Aisha ta ce" kinga Sarah ba abinda ya faru na san kanwata fiye da komai, Raudana ba zata aminta ta bakanta min ba, Na san kin ki fada min ne dan tsoron Allah Raudana, aman ina mai neman wannan alfarmar a wajen ki , ki kashe auren nan ya aure ni, ni zan fitar da mu daga kangin talauci, ni zan kawo mana sabuwar rayuwa , kema na biya maki karatu kasashen waje ki je ki cika burinki na zama hamshakiyar yar kasuwa, abanmu ya daina faskare kin ji? Rauda ta ce" ko? Aisha ta ce" Eh mana , Rauda ta yi murmushi ta ce" tohm Aisha ta yi murmushi itama, abin ya zo mata da sauki ma, Allah ya taimaketa har yanzu ba abinda ya shiga tsakaninsu ga dukan alamu Aisha ta waiga ta ce" ina tsinaniyar kishiyar taki ne? Rauda bata ce komai ba kawai kallon su take da mamaki, haka wai dama sukai rayuwa? Aisha banda son kanta da kin tsoron Allah bata ajiye komai ba AISHA ta ci gaba da fadin" zata gane kurenta ne idan na shigo tana ji tana gani Elhaj zai gagareta, domin soyaya idan muka fara baje kolinta ba shegen da ya isa ya raben min shi Rauda ji take wani abu na taso mata, mijinta na suna ne auntynta ke furuci haka kansa, idannuwanta ta lumshe ta ci gaba da jan carbinta tun karfinta rana neman natsuwa a wajen indalah Haka sukai ta tsara mata yanda zata kashe aurenta kuma su suna ikirarin ya auri Aishar, sai kuma abinfa ya tsaye mata irin yanda sarah ke ta faman wai yana ina ta yan shi, har ta fara cicira maganar ya ki zuwa ya gaishe su a matsayin su na yayunta Da ido kawai take binsu tamkar sabon kamu, sai kuma zuciyarta ta shaida mata *SUDAIS FA NAMA DAYA NE KWAL A CIKIN MIYA, MIJINTA* suna gamawa suka mike da niyar tafiya Wajen Hafsat ta je ta fada mata zasu tafi Hafsat ta fito tana waya da yayan su ya shaida mata kar Rauda ta saki ta fita, sannan ya umarci Hafsar da ta yi masu kyauta wada zata gigita su ...................wannan kennan...... *❣IDAN KA RAINA INDA KAKE❣* Na: *SAJIDA* *_LITATAFAN MARUBUCIYAR_* *_Duk Karyar kada_* *_Yar Mahaukaciya_* *_Neman na kaina_* *_Bani da zabi_* *_Daga tafiya daukar soja_* *_Idan ka raina inda make_* *🌈KAINUWA WRITERS✍🏼 ASSOCIATION*🤝🏻 ```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}``` https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation 5⃣3⃣ *ina mika godiyata ga mumbers Idan ka raina inda ka ke, ina jin dadin comment din ku fiye da tunanin ku, fatana na yi ta faranta maku kamar yanda kuke faranta min........* Fuska daure Hafsat ta miko masu envelope tana tir da Sarah, daman bata da mutunci har ta so yin kawance da ita? Sarah tana sakin wani malalacin murmushi ta ce" kawata ni kamar baki gane ni ba? Hafsat ta kaleta da kyau, ta juya ta ce" yana jiran ki zai raka ku kofa , Aisha ta kuga muryarta ta ce" aa, to ina Raudan? Hafsat ta yi masu banza ta shigewarta dakinta Sun dan jima nan tsaye sai gani suka yi kofar banban falon ta bude, Sojan nan ne ya bayana dan haka da sauri suka yi waje ya yi masu rakiya........... Rauda tana komawa dakinta ta zauna saman kujera mai zaman mutun daya, waje daya ta kurawa ido, magangannun Aisha ke dawo mata" ki kashe auren nan ya aure ni, ..... Na kashe aurena ? Auren da iyayena sukai min hudubar na yi biyaya ? Mijin da ta aureni ya aure ki? Ikon Allah, Aunty ai ana barin halal ko dan kunya, ke yayata wada muka konta ciki daya kece ke furtan kalaman nan? Takamarki ke kika fara son sa kin fi ni son sa? Kin manta ni kuwa ni ce *ZABIN DA ALLAH YA YI MASA?* ohk na bakanta ran kowa, uwa uba na sabawa Allahna dan na faranta maki wanda inada tabacin ba zaki taba gode min ba? Kanta ta girgiza ta dauko wayar ta tatara damuwar tunanin auntynta ta watsar a kondon shara tana furta a fili cewar" AUNTY ki yafe ni domin ba zan maki biyaya ba, HUMAIRA ki gafarceni domin ina son sannin ni kaina wai banzar ce ko kuwa? Sire, ka shiryi zuwa dan na dauki makamin tarwatsa du wani kudurinka .....ina son ganewa ina son sannin yar shila ta isa yanka kuwa? (🤔) Takarda ta dauko da alkalami ta zauna ta shiga rubuta dukan abubuwan da take bukata, tana yi tana murmushi domin abubuwa.ne na gyaran jiki na jiko, wanda ya rubuta abin ya ce ba lale budurwa ta sha ba aman ko ta sha ba wata damuwa du cikin gyara ne Tana gamawa ta mike ta ajiye ta fito ta nufi dakinsa kai tsaye Tana zuwa ta nemi izinin shiga Ya fito daga bayi ne ya saka kayansa yana kokarin shafa dan mai marar maski dan ya saba komai zafi sai ya shafa mansa mai kara gyara masa fata Karasawa ta yi tana masa murmushi ta ce" hi freind Tsareta ya yi da ido, kafin yake miko mata hannunsa na dama ya ce" asalamu alaiki freind Hannun nasa ta cafke tanai masa dan murmushi kafin take neman waje ta zauna kusa da shi sosai Yana gamawa ta dauko tea ta zuba ruwan zafi ta hada masa a dan kofi lipton da ananas ta mika masa Karba ya yi yana mai gode mata da idannuwansa Sai da ya gama sha , ya amsa kiran Samir a waya dan jin karfe nawa zasu je wajen daurin auren wani ma.aikacinsa Yana ajiyewa ya zo kusa da ita ya zauna ya ce" menene labari Hajiata? Ta kallo shi da kyau, a ranta ta ayanna haka fa , hajiarka bayan a ranka kanai min kallon yar shila ne Ta lumshe idannuwanta ta bude ta sauke saman kansa ta dan yi wasa da su kafin ta ce" freind, plz mana ina son zuwa saloon Kallonta ya yi da dan sauri, a ransa ya ayanna saloon kuma? Kai ina ba zai yiwu ba , a saloon din fa akoy maza, ko ba maza a ciki akoy masu yawo haka kawai a kale min mata? Ni mai yasa ma ban yi saloon a gidan nan ba? Yanzu da kawai sai dai ta leka a wanke mata kan a cikin gida hankalina konce Gannin ya yi shiru ya sa Rauda ta matsa ta dan shiga jikinsa ta ce" plz mana Freind, ina so ne na gyara gashina kuma tare da Hafsat zamu tafi ka amince min ka ji? Ta karasa tana mai tsare shi da ido tana marairaicewa tana dan kara shiga jikinsa Jin lunfashinsa yayi ya dan fara canzawa sakamakon hada jikinta da nasa da ta yi, a hankali ya samu ya janyeta daga jikinsa, ji kawai ya yi yana amsa mata da " to ku shirya idan an dan jima sai ku je Da sauri ta mike tana murna ta kara rungume shin kana ta juya da gudu gudu ta yi dakin Hafsat dan fada mata Baki sake ya bi bayanta da kallo, a fili ya furta" kai, ya aka yi haka na amin e mata fita zuwa saloon? Baya baya ya yi ya dafe goshinsa ya afka tunani, fadi yake ka ga Sudais ka farga daga rungumarka ka amin e mata fita? ( han ...) Shiryawa suka yi cikin abayoyi bakake Kamar yanda Hafsat ta yane kanta da dankwalin rigar haka ma Rauda ya kasance fuskokinsu kawai ake gani domin tsayi ne da ita hakama hannayen vudadu ne sosai Fitowa suka yi suna dan hirar su suna dariya kasa kasa, Sudais Da Samir ne zaune a falo an kawo masu jus da dan abin taba baki suna tataunawa suna jira lokaci ya yi su je wajen daurin aure Kanshin turarensu ya isar masu da zuwansu A hankali Sudais ya dago gabansa na dan faduwa ya ayanna what? Ita da zata fita me ya hadata da turare? Tsare fuskarta ya yi da kallo, batai kwaliya ko kadan ba, kwalinma tun na asuba ne da ta saka (wannan na daya daga cikin hudubar ma.aiki ga yarsa mafi soyuwa a gare shi wato nana Fadima cewa" du abinda kike kar ki bari mijinki ya ga idonki ba kwali😌 ( gyara ba laifi) ) A kasan zuciyarsa ya ayanna" MATA kina da tsararen kyau wanda idan kowa a duniya ke ganinsa zan ji haushi, bana son ki gane halin da nake ciki mata, A hankali ya dan dukar da kansa ya canza harshe wanda sun iso aman basa jin me yake fadawa Samir domin basu iya yaren ba kamar ruwa ruwa wato larabci, ya ce" Samir, zaka kai su saloon Samir ya dago yana kallon sa, ya ce" aman oga kafa yiwa mutumin nan alkawarin zamu je Sudais ya ce" eh zamu je mana aman sai an kai su na ga dawowar su kafin mu je Samir ya ce" idan aka daura auren fa Sudais ya hade rai ya ce" kai malan, idan na je nine alwalinsa ne? Ka ga ka yi min abinda zan samu nutsuwa, ba zan lamunci Hafsat ta tukasu haka sake ba kuma ba zan yarda wani garjejen direba ya ja min mata ba, dan haka kumu je tare mu kaisu Samir kam abin ya girmami tunaninsa dan haka sai ya amsa da kai kawai ya mike yana satar kallon Hafsat a ransa ya ayanna" ita harda su jan baki, idan na yi magana tace ai ita a kasuwa take, na saya na saya aman ta ki, kai gwara ma mu kaisun hankalina zai fi konciya ni din ma Hakan kuwa aka yi, Hafsat ce ta nuna saloon din da zasu je, suna zuwa Sudais cikin hade fuska ya ce" zamu je anguwa da mun dawo zamu biyo mu tafi gida Da toh suka amsa bayan sun yi godiya suka fice suka shiga saloon din Katon litafi mai dauke da kalolin gyaran gashi tun daga coiffure da kitso kala daban daban aka miko masu , Nan mai saloon din ta fada masu cewa ana gyaran jiki ana wankin kafa ana dilka da kurkum ana gashi idan suna so Kallon juna suka yi kafin Rauda ta dan saki murmushi ta ce" sis, ina gannin ko zaki je ki sayo mana sauran kayayakin nan ne ? Kin ga idan na je kar ya zama damuwa Hafsat ta karba tana karantawa, ta kali hajia mai saloon ta mika mata ta ce" hajia wannan kuwa a ina zamu samu? Hajiar na amsa tana karantawa ta ce" ai ina da su, sai dai nawa na kirki ne akoy tsada Hafsat ta yi murmushi tana zama ta ce" wannan ba damuwa bane, yanzu abinda muke so muna son dilka da kurkum, muna so a gyara mana kanmu, a yi mata turare harda wankin kafa Hajia tana murmushi ta ce" kawai ki ce a yi mata gyaran amarya Hafsat ta ce" yawa Hajia , sosai fa , ki baje komai kawai ki yi mana bilan Hajia ta kirayi biyu daga cikin yaranta suma matan ne masu kyau da su ta fada masu aikin da zasu kama mata Hajia datijuwa ce mai gyaran amare da saloon , ta kware a aikinta bata da dar ko wa zai zo ta san yanda zata tarbe shi ya koma da jin dadi samun abinda ya zo nema Na takaice Rauda ta samu gyara harda na mamaki, ba inda baya santsi a jikinta , hajia ta sameta ta kara bude mata idannu ta kara wayar mata da kai a wannan fannin duda bata san halin da take ciki ba, aman ta ganar da ira aure yakin mata ne kuma ta kara nusar da ita ko qa kake aure komai kyanka isarka kudinka mulkinka ke mace kece a kasa sai kin yi biyaya kuma kin yi hakurin zama da miji Sosai Rauda ta ji dadin wannan gyara, jinta take sakayau kafarta kuwa har wani zafi zafi take tsabar ta sha wanki akaifunta haka suke daukan ido tastastas Abu daya take maimaitawa wanda bayan hajia ta yi mata wankin kwakwaluwa ta cazata da kyau ta ce" sai fa kin cire kunya, ki tarairayi mijin Rauda sannan idan zama ya zauna ki sani kar ki zama irin matan nan wai su idan namiji bai neme su ba su sun dare wai a ja aji... wani ajin gare ki wanda ya fi ki kara kanainaye zuciyarsa yardarsa taki ce? Ke idan kika nunawa namiji kina ra.ayinsa zai ji shi tamkar wani sarki zai cewa kansa kai ashe nima namiji ne? Aman sai kin yi kokari kin cire kunya zaman aure kunya na wajensa Murmushi ta saki tana kallon hannayenta, ta kallo Hafsat ta ce" kai sun iya gyara, duba ki ga yanda fatana yake sheki Hafsat ta ce" ni kaina sun birge ni, kinga komai a waye sun iya aikin su Suna tsaka da labarinsu Wayar Hafsat ta yi ringing Tana dagawa Sudais ya ce :" ku fito Hafsat ce ta je ta biya suka dauki ledojin abubuwan da suka saya suka yi waje.... *❣IDAN KA RAINA INDA KAKE❣* Na: *SAJIDA* *_LITATAFAN MARUBUCIYAR_* *_Duk Karyar kada_* *_Yar Mahaukaciya_* *_Neman na kaina_* *_Bani da zabi_* *_Daga tafiya daukar soja_* *_Idan ka raina inda make_* *🌈KAINUWA WRITERS✍🏼 ASSOCIATION*🤝🏻 ```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}``` https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation 5⃣4⃣ Crêpe recette = *FULAWA, KWAI, , SIGA KADAN, GISHIRI KADAN, MAI, MADARA, BEUR* ki samu kamar kilo guda na fulawa ki saka masa kwai biyar🤗, ki saka dan siga da gishiri ba masu yawa ba ki daidaita daidai dandanon ki idan da chocolate zaki ci siga ya dan fi yawa idan kuwa da miya zaki ci gishiri ya dan fi sigan yawa, ki kada madara rabin kofi ki zuba, ki zuba mai ludayi guda ki kwaba fulawarki ki zuba ruwa ta murzu da kyau tamkar zaki yi kulin waina, shikenan sai kina toya abinki da beur zata baki crêpe kina linkewa 😋 sai ki yi mata yar dagargarar miyarta na yasa ko nikenken nama ko ki ci da chocolate Tunda suka kamo hanya Samir ya yi gum da bakinsa gannin ogansa ya daina jin yarensa, Ta madubin motar ya tsura mata ido, kanshin nan da suke bazawa fa? Sun yi nisa a tafiyar ya kali Samir ya ce" tsaya Samir ya kallo wajensa, ya ga yana nufin ya tsayar da motar ne Tsayar da motar ya yi Sudais ya fita ya zaga ta dayan bangaren.... Bude wajen direban ya yi fuska ba alamar walwala ya ce" ka je kawai zan karasa mu Wannan karin baki Samir ya saki, suma suka bi su da kallo domin muryar Sudais ko ya yi niyar yin magana a hankali girman muryar ke tona masa asiri sai an ji shi Samir kasa hakura ya yi ya ce" aman oga, me yasa toh? Sudais ya kallo shi da wani kallo mai kama da idan baka fita ba komai na iya faruwa Ceinture ya konce ya fita yana gyara rigarsa abin zaman mota yana kallon Sudais , da mamakinsa kiwa Sudais ya shige ya ja motar ya barshi nan baki da hanci a bude Hon din mai mashin ya zaburar da shi bai san lokacin da ya furta" kan uba🤔, toh oga na zuba hauka a gaban yarinyar nan yana ikirarin sai ma furta masa kalmar so zai nuna mata soyaya bayan du wani motsinta sai ya bayanar da kansa a fili, na tabata kishi ne ya konmace ya zama direbanta da mu shaki iska daya Yarinya Allah ya baki a gashe sai ki yi kokarin iya ci 🤣 Haka Samir ya dan taka kafin yake tsayar da mai mashin ya darw ya yi masa kwatancen gidansa, yana tafe yana mitar ai shima an dizga shi a gaban budurwarsa Yana tsayar da motar suka fita tare suna hirarsu da ledojin a hanayen su Hira ce suke kasakasa suna yar dariya, Da gangan Rauda ta ki tsayawa ta yi cikin gida abinta domin sai wani shan iska yake yana kakawar da kai karma su samu damar yi masa tambayar me ya sa ya tuko su ya tsayar da Samir ko kuwa su gano wani abin a tatare da shi, shi ya sa ya hade fuska tamkar an mare shi (🤣) Haushi ne ya mugun kama shi gannin yanda Rauda ta nuna halin ko.in kula, ita yar godiyar ma batai masa ba kamar yanda Hafsat ta yi masa Da mugun jin haushi ya kashe motar ya fito yana kokarin shiga wayarsa ta kwashi ringin ya dan tsaya ya duba mai kiransa managen kampaninsa ne dake Saudiya daya daga ciki ya sha kai ya leko ya jima rabonsa da su aman ya kasa matsawa har sai ya saka rana sai ya cewa kansa *ITA FA?* Yana gamawa ya shiga fallon , nan ya tarar da Hafsat na amsa waya ita faya dan haka ya kara hade fuska ya nufi dakin Raudar dan kuwa idan har ya kyaleta a irin wannan rainin na shiga wataran bama zata kula shi ba Da karfi ya tura dakin nata dan ta san ba da wasa ya zo ba Tsaye take ta cire doguwar abayar, ya rage mata daga ita sai dogon wando slim baki mai lafewa a jiki da breziya tana faman cireta ne itama dan ta je ta yi wanka ta yo alwallah sai jin bude dakin nata ta yi da karfi , ita gabanta har ya fadi ta yi tunanin ko Humaira ce ta shigo mata har daki yau kuma Daga shi har ita sai da gabansu ya fadi, Wata irin kunya ta ji ta lulubeta na gannin da yayi mata daga ita sai bra.......... Shi kuwa daskarewa ya yi a tsaye, shi bai karasa ya aiwatar da abinda ya zo yi ba, shi bai juya ba, kai kwata kwata ma bai yi magana ba Da sauri ta rarumi abin rufa ta yane jikinta tana jin yanda jikinta ke rawa ta tsuguna jikin bed hankalinta a tashe Da ido ya bita, har reaction dinta gaba daya yana kallonta, Jikinsa yake ji na rawarawa zufa na dan tsatsafo masa A haka ya yi kokari ya cira ya karasa kusa da ita, Damatsunan hannayenta ya kamo ya dago da ita ya matse mata waje har suna jin hucin juna *wai me kike boyewa?, an gaya maki ina ra.ayin hakan ne? Ki daina wani gudu dan kin gan ni koda ba komai a jikinki MATA, hakan na batamin rai bayan na fada maki dimniya sai ta nuna nake shanta*! Cikata ya yi ya fice a dakin da sauri ya nufi kofa da kys din ya bar gidan gaba daya Rauda a nan ta zube, jikinta na mata rawa, anya kuwa zata iya tarbansa gwa da gwa ? (Ai daman du budurwa kamila sai ta dage kafin ta iya hakan), Hannayenta ta cusa cikin gashin kanta dake fotar da fitinanen kanshi, ta kuma furta" na shiga uku ni Lalla, me ke damuna haka? Aman haka kawai zangar sai na tsaya masa a gabansa haka? Haka hajia ke nufi? Bata san cewa ban san komai na? Ya salam nima kar dai na yarda cewar yar shilar ce Ido ta lumshe kafin take yaye rufar ta je gaban madubi ta tsaya, A hankali ta share hawayen da ya zubo mata ta ce" ba shilanci bane kunya ce, wace an nanata min sai na yi da gaske da kuma tsoronsa, ga rashin sabo........... , kana nufin ko bani da komai ban isheka kallo ba? Kai sire zan gani Tsakanin wannan abin da ya faru an yi kwana biyu wani abin kirki bai shiga tsakaninsu ba, shi yana nuna fushi yake ne wanda ta lura yana da saurin hawa da kuma saurin sauka , ita kuwa ta bashi dama ne dan tana neman hanyar da zata kama shi a hannunta A haka har ranakun Humaira suka zo suka shige, suka kima zuwa suka shige Rauda batai gigin cusa kanta ba sai dan kawancen da suke na freind freind shima idan waje ya matse masu Bata wani adon jan hankalinsa dan ta lura yana cikin abinda yake sakawa da ya budi baki yake ce mata yarinya sqi dai abubuwanta da ta siyo ta hada tana dirkan abinta , ita dadinsu take ji sosai domin kuwa daga wanda da madarar peak sai wanda da zumuwa daya nema marar dadi wanda ake hadinsa da Madara peak da kabewa Sai sirika wa.inda take rubuta abinta da kanta ta hada da su kankana da sauran su, kaza kuwa dahuwa uku ta yi na kaza da ridi da nonon rakumi da suratul yusufa...............(SIRI NE) A yau ya kama ranar aikinta ne, ta tashi ta yi sallah ta koma bayi Wanka ta sallah na mamaki, tana fitowa ta saka iya pant ta dauki turare mai sanyin kanshi na humura ta samu ta shafa a jikinta cikin nutsuwa Tana gamawa ta konta saman bed dinta ta jawo sabon bargonta ta shige ciki ta yi lamo tana ayanna abubuwa a ranta Sai wajen karfe goma sha daya Hafsat ta shigo dakinta dan jin shiru yau bata fito ba Tana zuwa ta tarar da ita cikin bargo ta lulube ruf ko kanta ba.a gani ,.....ita ta samu bacinta ma Da sauri Hafsat ta hau gadon tana kiran sunnanta tana fadin lafiya? Rauda na jinta ta farka ta rike dan karta yaye bargon ta dan fitar da fuskarta tana kallonta , ta ja hanci kafin take yin atishawa , ta rarauta muryarta ta ce" mura ne da kasala ke damuna (😂 ciwon wata yarinya yar rainin wayo🤦‍♀) Da sauri Hafsat ta shiga jera mata sannu , ta fita dan nemo mata magani Sudais yana wajen aiki tun karfe 8 na safe shi da gidan sai da yama idan ya dawo da wuri karfe 6 dan haka Hafsat ta samo mata magani panadol ta hado mata shayi ta kai mata Da gangan Rauda ta ki sha ta langwabe jefi jefi takan dan satan kallon Hafsat du ta damu har ta ji ba dadi a ranta sai dai kuma ta ki mokewa ta ayanna idan har na ci ai zan daina kama da marar lafiya Wasa wasa har karfe hudu na yama Hafsat na fama da Rauda kan ko ruwan shayi ne ta sha , fir ta kiya tana langwabe hijabinta a gefenta sallah kawai ke tashinta tana gamawa take komawa ta lafe kan bed Hafsat ta dauki wayarta ta kuma kiran yayanta domin daman ta yi kiransa bai daga ba Can ya daga , Hafsat ta gaishe shi bayan salama , cikin nutsuwa ta ce" ya, aunty ce take mura ka biyo mata da magani Gaban sudais ne ya fadi, aunty? Wata auntyn ce ba lafiya? Bai iya tambayarta ba domin bai san irin tambayar da zai yi mata ba dan haka kawai ya kashe ya karasa office dinsa ya saita du abinda zai saita ya fito suka dauki hanya shi da samir Suna karasowa ya fita, wayarsa ma a nan ya bari domin jikinsa du ya yi sanyi, bai san waye ba lafiya ba Yana shiga ya tarar Fallon ba kowa, A hankali ya nufi dakin Humaira Ya tarar bata nan, Kansa kawai ya girgiza ya juya ya shiga na Rauda Tunda ya shigo da salama ta yi lakwas gabanta ya shiga dukan casa.in casa.in Karasawa ya yi har yana harde kafa ya ce" aa, ciwon ya yi zafi har haka ne? Tun yaushe Hafsat tana bashi amsa ya karasa bakin bed din, Hafsat na gannin hakan ta juya ta fita a dakin Sudais na karasowa hannunsa ya sa ya yaye bargon domin ta sake shi ya yaye shi gaba dayansa Saki ya yi yayi baya tagatagal tana kokarin rike wani abin, Bai san lokacin da ya furta " ya Salam, yana kokarin rufe idannuwansa sai dai ina sun tashi yau suma zanga zanga ba za.a hana su gannin abinda ke gabansu ba Rauda dake kokarin hana zuciyarta balowa ta fito ta samu a hankali tana kokarin tashi tsaye, ta mike ta sauke kafarta daya tana kare kirjinta da hannunta ta mike tsaye da nufin zata dauko wani abu ta rufe jikinta dan tafia ta yi luuuu dan haka ta saki hannayen nata dan tare kanta kar ta jibgu a kas a ranta kuwa tana ayanna kar a je daga wasa ciwo ya zamo min gaske (haba Rauda a wuni ba.a ci ba ai an dan ji jiki ba azumi ba ba komai ba ) Sudais ya daga kafarsa taku daya ya yi ya rikota karta fadi, maimakun ya kaita saman bed dinta sai ya jawota jikinsa ya ........... *❣IDAN KA RAINA INDA KAKE❣* Na: *SAJIDA* *_LITATAFAN MARUBUCIYAR_* *_Duk Karyar kada_* *_Yar Mahaukaciya_* *_Neman na kaina_* *_Bani da zabi_* *_Daga tafiya daukar soja_* *_Idan ka raina inda make_* *🌈KAINUWA WRITERS✍🏼 ASSOCIATION*🤝🏻 ```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}``` https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation 5⃣5⃣ Wani irin riko ya yi mata ya hadeta da kirjinsa ya saka hannayensa biyu ya riketa ya lumshe idannuwansa ya kasa aiwatar da komai sai kara rukunkumeta yake yana shinshinar fitinanen kanshin da take fitarwa mai neman zautar da shi A hankali yake kara riketa wanda ita kuwa ta rikice sanadiyar sajensa dake shafar wuyanta (🙈 saje🥺) ga uwa uba pant din nan na jikinta shi ne ba komai sai shi Murya na rawa ta ce" wai wai meye haka sire? Ni ba sire din ki bane Ya fada muryarsa a cunkushe Gaba daya karfinta ta saka dan banbare shi a jikinta sai dai ga mamakinta ko motsi bai yi ba gashi jikinsa sai kara daukan bari yake hakan ya sa har itama jijiga take sosai Gannin tashin hankali na neman samunta, daga neman gira zata rasa ido , daga wasa yana neman zame mata kurma sannan makaho kuma wanda baya ji idan an taba shi ya saka ta dadage ta saki kuka tana rukunkume shi ta cusa fuskarta a kirjinsa sosai dan ya farka daga inda yake faman zuwa Ta yi sa.a domin kukan nata ya sauka a kunnensa a daidai lokacin da yake kokarin kai hannunsa wani sashi na jikinta dan tabatarwa shin da gaske nata ne? *Ka bari na roke ka,* Rauda ta fada muryarta na rawa hawaye ya wanke mata fuska sannan jikinta ya dauki dumi na rashin lafiyar gaske Sudais ya dan sasauta mata rikon da yayi mata na farko, zuciyarsa kuwa dokawa take tamkar ta balo ta bar gangar jikinsa, a hankali ya dago hannunsa na hagu wanda tun daga tsintsiyar hannun jijiyoyin jikinsa sun mimike sun yi wani birde birde da su ya samu ya dan tsayar da barin da yake ya dago habarta , dayan hannun kuwa ya rike tsintsiyar hannunta na hagu da shi , Idannuwanta a lumshe Suke tunda ta ji yana kokarin dago da habarta, yana dagowa ya tsare fuskarta da kallo Hawaye ya wanke fuskar , girar idannuwanta sun jike sun yi lumtu , sai lebenta da ya yi jajir yana rawa dan tsabar tsoro Cikata ya yi ya nufi bakin bed dinta ya yiwa kansa mazauni ya tsareta da ido yana binta da kallo ba kunya ba kyafta ido ita kuwa du ta rikice tana neman abinda zata rabawa jikinta Hijab dinta na sallah ta ja ta saka a baibai dan tsabar rikicewa tana dan sosa kanta tamkar mai wani kwari ko dati a ciki Idannuwansa a lumshe suke tamkar wanda ya rufe su shi kuwa binta ne yake da kallo , ya kasa yarda cewa wai Raudansa ce haka, aa, saurin girma ne ta yi haka ko me? Pant dinta shi sai ya ce karshen girma ne duda haka bai rufe mata jikinta yanda ya kamata ba, sambala sambalan cinyoyinta ke yi masa yawo a kwanya, shafafen cikinta da ya hade da jikinsa ya fado masa hakan ya sa tsikar jikinsa ta kara mimikewa, sai mutanensa, ido ya lumshe ya kara lumewa a kogin yabo, aa, Humaira kirjinta tamkar bera domin humaira tsaye take ba tudu ba gangare , matar amana kuwa wato khairath ta kasance mace mai jiki sosai, wani lokacin jikinta ke hana ta yin wani abin To aman Rauda fa, ko daman kafin budurwa ta kai shekarun Humaira haka halitarta take? Kai ina halita halita ne, A hankali ya kara bude idannuwansa ya sauke a kanta, a ransa ya ayanna" wayo ki cire A fili kuwa sai ya miko mata hannunsa yana nufin ta zo Rauda ta rufe idonta ta ki daga kafarta ko daya tana fadin ba zan iya da wannan murjejen katon ba, abubuwan da Aunty ta fada ba zan iya ba, haba kai wannan a hakama ya hautsine min ina da Sai kuma ta yi gagawar rufe bakinta ta bude idannuwanta tana zaro su Tsaye yake kusa da ita sosai daf da ita, Hannayensa ya saka ya daukota cimak daga tsayuwar wanda hakan ya saka ta shiga haharba kafaduwanta tana kara jimke damatsunan hannayensa dan kar ya kayar da ita (ke firit🙄) Fita ya yi a dakin nata ya nufi nasa da ita Yana zuwa ya yi mata masauki saman bed dinsa wanda tunda ta zo gidan bata taba hawa samansa haka ba Ganninta du a firgice ya saka Sudais ya yi murmushi a ransa ya ce" Sudais ga dama fa, kar ka bari ta dagoka a haka A hankali ya shiga dan shafa gashin kanta kafin yake dukawa sosai kusa da kunnenta , Sai da ya shaki kamshinta mai saka shi nutsuwa ya ce" ki daina wannan tsoron mana hajiata, abin tsoron na gaba sai kin iya dauka kafinnan Yana gamawa ya cikata ya nufi bayinsa yana tafiya a haharde wanda Rauda bata gane dan me yake tafiyar haka ba sai dirowa da ta yi daga saman bed din , Bata san lokacin da ta furta" *TAP* Hararen bayin take tamkar ta shako shi ta ji wai yarintar me ta yi haka wanda a irin wannan kasadar da ta yi aman bai gani ba har ya furta mata haka? Rauda kin saki kanki da yawa, ke kike nuna masa tamkar wani sonsa kike har da yake kokarin samun damar ya murza maki rashin mutunci, da kin ja ajinki, kin bari shi ya fara nunawa sai ki yi fito na fito da matarsa, aman a haka ke a wa kare da gudun laya? Tsaki ta ja lokacin da ta ji saukar shower, kwatakwata ma sai ta ji zazabin ya saketa, ta zabgawa dakin harara ta juya ta fice tana fadin ni da kai kyasashe ya kasa Lokacin da Sudais ya fito ya ga Rauda bata nan ya dauki wayarsa ya yi dealing number Hafsat Tana dagawa ya umarceta da ta je ta kira masa Rauda ya yi kiran docter Yana kashewa ya dafe kansa ya kali agogo, a kadan ya kwashe awa a bayi kafin ya samu ya iya daga kafarsa, yarinyar nan sai ta kashe shi da alama, ita bata gane yana daga mata kafa ko? Zama ya yi bakin bed din da tawul a kugunsa wayarsa ta yi kara Dagawa ya yo domin hafsat ce Hafsat ta ce" yaya, wai ta ce ita ta warke Shiru ya yi , kafin yake datse wayar Dan tsaki ya ja a fili ya ce" dadina da yaro, ko me ka yi da shi sai yayi maka yarintar, ita fushi ta yi ko me? Ohk so rake na zauna a yannayin nan ina kallonta tana kara birkita min lisafi nima na konta rashin lafiyar ko? To kar ki ni sai na zo da likitan ta duba ki 😑 Tare da docter suka shiga dakin Rauda wace ta yi ruf da ciki har zuwa lokacin ranta a bace yake da abinda ya kara fada mata, sannan ta dora laifin gaba daya a kanta tana jin haushin kanta ne Murmushi docter ta yi gannin yanda Rauda ke hade rai tana jujuyar da kai Docter Amina ta ce" kai sire ko dai Zamu samu baby ne? A tare suka kallota Ita Rauda ta yi mata kallon ka ji wani rainin hankali baby ta ya? Shi kuwa ya yi mata kallon mamaki, baby fa? Abinka da wanda baya rike magana ko da zafi ko akasin hakan sai ya girgiza kai ya ce" kai docter Amina kema kina da abin dariya, *itama ai babyn ce!* Kwal uba ! Shine kalmar da zuciyar Rauda ta fada Da ido ta tsare shi tana kallon sa, To a yau ita ta fahimci me yake nufi da ita, Tabas tsananin kiyayarta ne ya saka shi bai kulata ba kuma baya jin kunyar fadi ( eyah Rauda hali ne, mai irin halin ba abinda ya dame shi magana ko a gaban wa zai iya furtata ne kai tsaye sai dai du abinda za.a yi a yi) Docter Amina ta bada hankalinta tanai mata tambayoyi aman Rauda ta tsare Sudais da kallo zuciyarta na dokawa tana tunanin abinda ya dace da shi Sudais Hankalinsa ya tashi, shima kallon nata yake kafin yake matsawa kusa da ita, muryarsa ya sasauta ya ce" WHAT HAPPEN MATA? ksllon da ta yi masa ya sa ya salami Docter da fadin zai kirayeta Docter na fita ya juyo ya miko hannunsa dan kamota ya ji me ke damunta Rauda da murya msi kama da bacin rai ta ce" don't touch me! Idannuwansa ya wara yana kallonta, wai me ke dammun yarinyar nan ne har haka? Rai bace ta ci gaba da fadin" ba sai ka fadawa kowace banza cewar ba abinda yake tsakanina da kai za.a fahimci cewar ka tsane ni! Ba sai ka baza ni a duniya ba za.a san ruwa ba sa.an kwondo bane, da ba dan Allah da hukuncinsa ba da sai na ce aurenka ya yi min shishigi, ka gane nima ba sonka na...... Saurin dora yatsarsa ya yi a kan lebenta ya rufe idannuwansa ruf, Zuciyarsa ya kai hannunsa na dama ya dafe da dan karfi kafin yake bude idannuwansa ya jefeta da marayan kallo mai cike da ma.anoni da dama Idannuwansa ya lumshe ya bude nan da nan idon ya hadu da ruwan kwallah A hankali yake jan hannun nasa daga kan lebenta yana kallonta irin kallon nan mai sakawa zuciya ta doka tun karfi Yana dan girgiza kansa yana ja da baya da baya stil bai sauke hannunsa daga saitin kahon zuciyarsa ba har ya kusan fita a dakin inda ya bar Rauda tsaye itama tana zubar da kwallah, Yana fita ta silale nan ta dafe kanta ta ce" ya Allah, ka fahimtar da ni abinda ke duhu a gare ni Sudais na fita ya fice a falon ya fita can baya wajen gardin, kansa ke sara masa da mugun karfi inda jikinsa ya yi masa nauyi, har zuwa wannan lokacin bai saki dadai zuciyarsa , Hafsat da ta ga fitarsa a haka ta biyo bayansa da sauri dan ganinsa yana rike da kansa ta yi gagawar karasawa kusa da shi tana dan rike hannunsa hankali tashe ta ce" yaya, menene? Lafiya? Me ke faruwa? Sudais da kyar ya samu ya rike hannunta, muryarsa na wani iri ya damki hannun nata ya ce" tabas na afka a jarabawar rayuwa, subahanallah, astagfrulah, Hafsat *Bata sona* , bayan du irin tarin son da nake yi mata, Hafsat *ina son Rauda mudin raina* Hawaye ne ya taru a idannuwanta, tana kallonsa da tausayu, wani lokacin me ake da murdaden hali, kafiya batai ba, Ta sasauta murya ta ce" ka sanar da ita ne yaya? Cikin bacin rai ya ce" Sai na fada mata ne? Wa na taba fadawa? Sai ita? Aikina, yannayin jikina, dabi.una a kanta basu isa su nuna mata ba? Sai na waka? Sai na yi ihu? Ko sai zuciyata ta fice ta bar gangar jikina hankalinta zai konta? Wa ke koya mata? Yarinya ce ke kanki kin girmeta sosai, tunaninta bai isa ya bata wannan abubuwan ba, bai isa ya sakata ta ringa wahalar da ni ba, ya take so da ni ne? Hafsat da hannunta da ya jimka ke mata zafi ta ce" yaya , ai *mace malamar kanta ce komai kankantarta*, Ta dan ja hannunta aman bai saki ba, ta sauke ajiyar zuciya ta sasauta muryarta ta ce"'"" Ba yawa😌 *❣IDAN KA RAINA INDA KAKE❣* Na: *SAJIDA* *_LITATAFAN MARUBUCIYAR_* *_Duk Karyar kada_* *_Yar Mahaukaciya_* *_Neman na kaina_* *_Bani da zabi_* *_Daga tafiya daukar soja_* *_Idan ka raina inda make_* *🌈KAINUWA WRITERS✍🏼 ASSOCIATION*🤝🏻 ```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}``` https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation 5⃣6⃣ Hafsat ta ce" yayana, ita fa mace komai kankantarta ta san abubuwan mamaki, Rauda a wajenka kanai mata kallon yarinya aman a duniya inda mace ta kai har shekara 22 ai ba yarinya bace , ka yi hakuri, ka dani zuciyarka, ka yi kokari ka samawa kanka natsuwa yayana i beg u Sudais yana kallonta, can kuma ya cika hannunta ya yi gaba ya kara kutsawa cikin lambun yana lanyi Da sauri Hafsat ta daga kafarta zata bi shi , sai dai cikin daga murya ya ce" kar ki biyo ni, ki je kawai Juyawa ta yi da sauri ta koma ta dauki wayarta tana kuka ta yi kiran Samir Samir dake zaune gaban cimarsa zai ci ya ji karan wayarsa, A hankali ya dauko yana duba mai kiran Da sauri ya daga yana mai jin dadin gannin sunnanta tana kiransa Yana dagawa cikin muryar kuka Hafsat ta ce" ka zo plz yaya Samir Zumbur ya mike , ya ce" Hafsat, menene? Hafsat ta kashe bata bashi amsa ba ta saka abayarta ta lulube jikinta sosai ta dan fesa turare ta fito tana tura baki dan me zai tsaya yanai mata tambayar menene bayan ya ji muryarta hankalinta ba a konce ba Ya kai minti talatin tsakani kafin Samir yake yiwa gidan oga Sudais dirar mikiya Yana kokarin karasawa ya ci karo da ita wajen motoci ta rungume hannayenta da alama shi take jira Gabansa ne ya fadi yana mai yi mata kallon bege har ya karasa wajenta, Tun kafin ya yi magana ta tarbo shi yannayinta irin na dazun dai ta ce" na rasa ya zan yi da su, yaya ya cika naci kan abu bai san wannan karon ya fado kan macen da kudinsa ba zai saka ta rufe ido ta yi ta binsa ba duda irin talaucin da suke ciki kuwa, Ya kasa fahimtar hakan ya sake mata ya furta mata kalmar so din nan ya ga idan ba zata kulashi ba, sai dai ya ringa fama da kansa haka? Bana so ya kamu da rashin lafiya ya Samir Tunda ta fara zuba ya sauke nanauyar ajiyar zuciya domin ba abinda bai saka a ransa ba ciki harda ko an yi mata miji? Harde hannayensa ya yi, a zuciyarsa ya ayanna ashe tana magana har haka A fili kuwa ya ce" ya kike so na yi yanzu? Hafsat ba tare da ta kali yannayinsa ba ta ce" bana so ya fadi rashin lafiya, shi gare mu, shi muke ganni, ka saka shi ya tunkareta, du isar yaya na ga halamar tsoronta yake, idan kuwa ba haka ba ya cirewa kansa irin damuwar dake damunsa Samir ya girgiza kansa, ya kawar da kai ya ce" hum idan tana magana tamkar ita ba fada mata sirin zuciyar tawa na yi take wahalar da ni ba To bara ki ji hajia, Allah ya fi ku ke da ita, idan Allah ya yarda ba zaku hadasa mana rashin lafiyar ba tunda har kun san ilar hakan da gangan kuke Yana gama fada ya juya ransa a bace bai kara koda kalma daya a hakan ba Baki sake tamkar kofar wambai Hafsat ta bi samir da kallo, Tana kallo ya shiga mota ya tayar ya juya da mugun gudu ya bar gidan Hannunta ta kai ta kama habarta ta dama ta ce" toh fa Haka Hafsat ta yi ta tsayuwa a wajen motocin nan inda ta ga yayanta ya dawo ya wuce ba tare da ya ce mata komai ba shima Ajiyar zuciya ta sauke ta dauki aniyar wannan lamari zata kai shi wajen Allah kawai Allah ya yi maganin hakan Sudais bai zame ko.ina ba sai dakin Rauda Yana shiga ya tarar da ita konce kan bed dinta A hankali ya cire hiramin bisan kansa, ya rage masa rigarsa da wandonsa a hankali ya karasa ya hau bed din Garu take kallo dan haka ya samu damar rungumeta Ajiyar zuciya ya saki yana shafa kanta a hankali ya ce " ya aka yi bakya so na mata? Rauda ta yi shiru tana jinsa a cikin jini da bargonta, so? Tana sonsa kai fiye da tunaninsa, irin jayayar da ta ga ana yi da shi ya karkato da hankalinta bisa kansa har ta dasa ayar tambaya a kansa, sanu a hankali ta ringa karantar qualities dinsa manya manya wa.inda sun isa su saka a so shi Har ta jita taunbul a cikin kogin kaunarsa ba tare da ta ankara ba , Ta ji burinta ya lura da ita, ya sota , ya daina kallonta a matar sadaka Lamo ta yi a jikinsa ta kasa furta masa komai Kin san meye? Kalmar nan tana da girman da zata iya tsayar da numfashina mata, idan kina furtan kalmar ki nakan ji iskar duniya ta yi min kadan wajen shaka, Jin magangannunsa take a can kasan kokon zuciyarta hakan ya sa cikin nutsuwa ta ce" me ya sa? Sudais ya yi shiru still idannuwansa a lumshe Rauda ta samu ta juyo da kyau tana kallonsa, ta ce" me ya sa ba zan kai ka so ni ba? Me ya sa darajata bata kai ka boye abinda ke tsakanina da kai ba? Me kike nufi? Sudais ya tambaya yana mai tsareta da dara daran idannuwansa. Rauda ta ce" ina son sanin me ya sa kake kwatantawa kowa ni din ba kowa bace? .Sudais ya rintse idonsa Rauda ta ci gaba, ko dan ni din ba kowa bace? Bata kai karshen kalmarta ba Ta ji saukar leben Sudais saman lebenta Duf maganar bakinta ya dauke sakamakon irin yanda yake kissing dinta sannan ya rukunkumeta a jikinsa sosai Ya jima yana aika mata da sakon nan kafin yake sasautawa Ya bude idannuwansa da sukai jajir ya sauke a kan fuskarta nan ya ga nata idannuwan a rufe suke ruf Murya a shake ya ce" na yi tunanin zaki karanta ba sai na fada ba *RAUDAT* na zauna a nigeria na tsawon lokacin nan ne dan ke Da sauri ta bude idannuwanta , dan ni kuma? Eh dan ke Rauda, du abinda zai nisanta ni da ke koda neman kudina ne na tabatar maki zan shure shi da kafana Kifta ido kawai take tana kallon lebensa yana zaro kalamai cikin tsari A hankali ya kawo irannuwansa cikin nata ya ce" tausaya maki nake shi ya sa ban baje maki irin abinda ke damuna a kanki ba Da sauri ta sada kanta gabanta na dokawa, yana nufin yana sonta? Hannunta ya kamo mai dumi ya kai daidai kahon zuciyarsa, ya sasauta murya ya ce" ki ji kaina, ki so ni kodan kwayar zara ne, ki daina ambata min kalmar ki, ki yi min so koda na matsayina musulmi dan uwanki , na san a hankali zaki so ni a matsayin namiji, Mata bani da kyau ne? Me ya rage ni? Rauda ta cusa kanta cikin kirjinsa tana sauke ajiyar Zuciya Sudais ya sakata a jikinsa sosai ya ce" *Bana iyawa sai da ke*, Yana gama fadin haka ya shiga aika mata da wasu irin zafafan sakwanni, sakwannin girma ne da su, sakwannin sun dirowa Rauda a ba zata ne, Bai so ya bude mata filin nan ba, zuwa ya yi ya dandanna miyar kawai sai dai abubuwan da ya fara karo da su suke kara kayatar masa da tsarin tuwon, a hankali ya fara manta abinfa ya kawo shi ya shiga kokarin kaiwa tuwon nan loma kima kima, Kokarin yiwa abincin fila fila yake, ya dadafe ya ware karfinsa yana saukewa tuwon nan dukan gajiyarsa Abu ne ya ci karo da shi bako kuma sabo a rayuwarsa kusantar matar sunnanrsa mai tsafta, jikinta du santsi, komanta cascas ne🤣🙊🙈, wannan lamari ya saka shi sakawa kowani lungu da sako albarka ba tare da ya yi kauro ba Wayo Raudana🤣 *❣IDAN KA RAINA INDA KAKE❣* Na: *SAJIDA* *_LITATAFAN MARUBUCIYAR_* *_Duk Karyar kada_* *_Yar Mahaukaciya_* *_Neman na kaina_* *_Bani da zabi_* *_Daga tafiya daukar soja_* *_Idan ka raina inda make_* *🌈KAINUWA WRITERS✍🏼 ASSOCIATION*🤝🏻 ```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}``` https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation 5⃣7⃣ A wannan rana Sudais ya dagargaji Rauda tamkar ya samu wace ta jima a harka, bai yi haka dan son ransa ba sai dan irin duniyar da ya hadu da ita ya kasance ta kanainaiye shi saima yana shirin barinta sai ta kara kayatun masa ta rike shi taf Bayan komai ya lafa da wajen minti ashirin Sudais ya bude idannuwansa ya sauke kan Rauda Idannuwanta a lumshe suke sai dai sun kumbura na tsabar kuka fuakar ta yi jajajir A hankali ya mike ya bude wajen tawul dinta ya dauko guda ya nufi bayi Wanka yake aman hankalinsa na wajenta, shi bai san me zai ce ba, ya gama dimaucewa ya gama fita hayacinsa ya yi saranda ya sarawa Mata, aa ya ilahi daman haka lamarin yake ko dai ita ce a kanta.........? Subahannalah lamarinta ya girgiza shi, Wai shi dake cewa Humaira idan tana jajan ya aka yi idan suna raya sunna baya kuka kamar yanda ta karanta a wajaje da dama maza na kukan hakan sai ya ce mata haba dai sai kace wani dan daudu? Yau sai ga shi yana zubar da hawaye a saboda mace? Menene sirin nan ne? Daman zai ga wannan ranar? Ashe ya jima yana cutar kansa yanai mata kallon baby ta nuna Murmushi ya saki kafin yake maida hankali ya yi wanka ya fito dan kar yayi ta tunane tunane a bayi Kayansa ya mayar ya zame saman salaya yana kallon agogo, lokacin sallah ya yi har ya dan huce dan haka ya tayar da sallah, A sujadarsa ta karshe bayan ya yiwa iyayensa adu.a da neman gamawa da duniya lafiya da shi kansa da kuluhin musulmai sai ya tsinci zuciyarsa na kai kukanta wajen Allah cewa" ya ubangijina, kai ka yi ji ka yi ta, kai ka san sirrin dake tare da ita, ya Allah ni bawanka ne bani da karfin yin komai sai wanda ka yi min, Allah wannan jarabawa ta soyayar yarinyar nan a raina ya Allah ka sa itama ta so ni, ka bamu zaman lafiya baki daya Allah ka yiwa *MATA* albarka Haka ya mike ya yi tahiya ya gama salarsa ya jima yana adu.a kafin yake hango tana dan motsa abin rufar da ya dan rufa mata da alama dai ta dan fara saukowa Shafa fatihar ya yi ya mike ya nufi inda take da dan hanzari Yana zuwa ya shiga kokarin taimaka mata Cikin muryar kuka ta ce" wayo karka tabani, kar ka tabani ka bar ni Ta karashe tana mai sakin kuka mai cin rai A hankali ya saki abin rufar, ya fan duko saitin fuskarta , murya a raunane ya ce" ki bari na taimaka maki kin ji MATA? Rauda ta kawar da kanta cike da kunyarsa, ina ai an yi daya ita ba zai kuma ganninra bama, taf dama haka ne? Kai aman mata basu san ciwon kansu ba, da wannan wahalar ne suke yiwa kishi? Saboda wannan abin ne suke tashin hankali? Ita dai bata suma ba aman ta gwamace a sume ya sha shagalinsa idan ta farka sai ta yi jinya, aman cikin ikon Allah tana kallonsa yana kallonta yana faman yi mata surutun itace numfashinsa aman kuma yana faman rabata da shakar na duniya, wannan mutun ya san lagon keta, aman abu daya ya tsaye mata lokacin da hawaye ya zubo masa ya rukumkumeta ita dai bata san ko wani wajen nasa ne kuma yayi masa zafi ba a lokacin ya ce" *i love you* kafin yake jibgo mata a jiki Itafa so take ta samu ta ga ta mike irin dandatsar da jikinta ke mata ta tabata wani wajen ya bale Ki yi hakuri, Sudais ya fada yana mai dora tafin hannunta saman fuskarsa sajensa na shafar tafin hannun nata , ya kuma tausasa murya ya ce" ni ne ko? Rauda ta kikifta ido tana kallon wani wajen, ita fa ba zata iya hada ido da shi ba, haba shi ko kunya? Ko kunyarta baya ji? Haka jibgege da shi? To tunda ba zaki kula ni ba , bara na yi kiran momy ta taimaka min ta zo, ita ai idan ta zo zaki kulata Ya fada yana mai mika hannunsa wajen telephone fix dake ajiye a gefen bed dinta Kasakai ta yi ta saki baki tamkar sakara tana sauraronsa lokacin da daram take jin muryar mamansa ta dauka tana amsa gaisuwarsa Ita dai bata san yanda aka yi ba sai ganinta ta yi gabansa ta damke telephone din ta ajiye hakan ya sa kiran katsewa Sanyin ac din da ya huri jikinta ya sa ta tuna halin da take ciki na rashin sutura a jikinta Da sauri take kokarin juyawa sai dai ta makaro, Sudais dake sakar mata murmushi ya dauketa cimak ya nufi bayi da ita wanda hakan ya sa ta rufe idannuwanta tanai masa kuka har ya karasa shigewa da ita ya maro kyauren dan kar na ga me za.a yi a ciki😔 ........... .......gidan aunty........ A yau Elhaj mijin aunty mahaifin Sarah yake dawowa daga tafiyar da yayi ta harkar kasuwancinsa Tunda safe ake shirye shirye kowa na kimtsa kansa domin mai saita masu zama zai dawo, kananan yayansa du sun yi zuru sun afka tunanin tashin hankalin mahaifin nasu domin kuwa koda wasa suka kuskure sai an karbe su a hannunsa bai iya duka ba, ba baba ba karami kuma idan ta hado ki da shi zai wulakanta ki ne a gaban yayanki ba abinda ya dadasa da kas, sannan yakan dauki yan aiki iya bangarensa aman fa ba aiki kadai suka tsaya ba, idan ke balagaza ce za yana rudarki yanai maki wayo kina bashi hadin kai da ya gama morar ki zai kore ki ne ba ko sisi, idan kuwa kin san ciwon kanki kina nuna masa aa bama zaki kwana a gidan ba zai salame ki bayan ya gagaya maki magangannu masu daci ya yi maki korar kare har ya hada da shari sai idan Allah ya fida ke Bangaren aunty ma du sun kama kansu Aisha ta koma dakin Sarah dolenta domin da dakin laurw fitina ta koma gara ta kwana tana jin minsharin laure da ta kwana tana jin badalar da Sarah ke yi, duda yanzu sun dan sasauta mata rashinutuncin aman a halayanta ba abinda ta canza, Hankalinta ba a konce yake ba da ba dan koda yaushe sai ya dauraye gidan dan gannin wa ke nan wa baya nan barnar me akai masa da sauransu da sai ta yi ta zamanta har Rauda ta yi kiranta sai ta koma gida wajen su mama sai dai kash Aunty ce zaune an sha kunshi, an sha kitson tarban miji ta hakimce ta kashe kudi ta ajiye layan miyar da zatai masa girki gobe domin yau ba ranar girkinta bane Sun cika dare suna zaune da Sarah jin shiru suka mike sukai dakunansu domin sun yi tunanin ko ya fasa zuwan ne yau Can cikin dare Aisha ke jin gurnani , gabanta ya fadi ta juya ta ki buda idannuwanta don karta yi mugun gani Abin ya ki fasawa ta dauki filo ta dora a kanta dan ta daina ji sai dai ina sosai take jin kukan iya shegen da Sarah ke aikatawa Mikewa ta yi ta yi falo domin kiwa ji take kamar numfashinta ya tsaya dan tsoro da mamaki , Sarar dukantama ta nawa ce har ta dorawa kanta irin wannan rayuwar Falo ta dawo ta nemi waje ta konta tana adu.a ta rufe idannuwanta a hankali dan samu ta huta domin kuwa dare aka ce mahutar bawa Bata jima da konci ba barci ya kwasheta domin a gajiye take tina Can cikin bacinta take ji ana shafa bobs dinta da dan karfi karfi Hannunta ta kai irin baci yayi nauyin nan dan kore abinda ke yi mata tafiya a jiki Sai dai me ji ta yi an juyota dan haka ta bude ido da sauri ta sauke a fuskar mutumin, Bakikirin ne a fuskarsa bata ga annuri da haske irin na musulunci ba Idannuwansa jajajir sai fitar da harshe yake tamkar tsohon maye yana tanda yana kokarin kara kai mata cafka Ihu Aisha ta saka tana kokarin diro kafafuwanta a kan kujerar tana zaro ido domin harga Allah bata san ko waye ba haka bai yi mata kama da mutun ba gajere ne mai kakauren jiki ga alama sam ba wani hasken musulunci a tare da shi Ke zan ci uwarki ni zaki yiwa ihu a gidana? Wacece ke? Uban me kika shigo yi a gidana? To ko aljana ce ke yau sai na kai ki kas dan uwarki Yana fada ne yana kokarin kara afka mata wanda ta takarkare tana kwala ihu iya karfinta tana zile masa shi kuwa yana kara binta tamkar zakin da ya jima da yinwa fadi yake ki tsaya ba zan jima sai na barki a gidana Aunty ce ta ce " Elhaj lafiya? Elhaj ya juyo ya sauke idannuwansa kan aunty, wani haushi ne ya turneke sa , da zafin rai ya ce" ke kuwa uban me ya fitar da ke? Aunty dake kallon yannayinsa ta mayar da dubanta wajen Aisha dake tsaye jikinta na bari tamkar an jona da wuta, gabanta ya fadi bata san lokacin da ta furta" ke kuwa uban me kike yi a waje Aisha? Aisha da mamaki take kallon aunty kafin ta ce" aunty, kin gani taba min jiki ne yake wannan mutumin Aunty dake kokarin dora laifin kan Aisha sai ta ce" sai me? Nace sai me? Da me ya fitar da ke in ba ki ja ra.ayinsa ba? Sai da na fadawa Sarah ba zata kwana ba aman tace ita aa sai ta kwan ni ban santa ba kawar sarah ce Sarah dake tsaye ra harde hannayenta ranta ya bace, a ranta ta furta ji moms du ba ke ke kara jawota ba dan cikar burinki? Burinki mana dan na auri elhaj Sudais ke kuwa ki samu fada a wajen aba aman shine zaki dora laifin a kaina tun ba.a je ko.ina ba? To bara ki gani Karasowa Sarah ta yi ta ce" babs sannu da zuwa dai, Kar ka damu yanzu zata tafiyarta kawai dama taimako na so yi aman ta je kawai Aunty da Aisha a tare suka kali Sarah wace tana gama fada ta juya ta yi shigewarta ba tare da ta kara tsayuwa ta ji wani maganar ba Elhaj kuwa ya buda wuta fadi yake karuwa gidan iyayenki ya gagare ki shine ni za.a zo a zube min masifa ko? To maza fice min Yana masifa yana komai ya rakata har mai gadi ya bude gida ya ingizata tana waiwaiyen aunty tana ihun kar a fitar da ita a bari tsafiya ta yi tana rusa kuka tana magiya aman ina aunty sai kawai ta sada kanta ta juya haka mahaifin sarah ya fitar da Aisha cikin talatainin daren nan domin karfe hudu na asuba ne ya makawa gidansa kyaure yana haikar baki wanda daga lokacin ba wanda ya koma barci dan kuwa ya tayar da kowa da masifarsa kuma ya kafata a tsakar gidan sai aibata matan yake da yayansa......... (🤦‍♀) Aisha kuwa tsaye ta yi jin wani sanyi na surarta, bata fito da ko dan kwali ba bale takalmi, kale kale take nan da nan wani mugun tsoro ya dirar mata gannin ba haske sai na farin wata wanda a lokacin bashida hasken nan ya rage, Kukan kare take ji yana yowa wajenta kafin take jin ihun janki shima yana irin kukan nan .......jikinta ta kankame ta toshe bakinta dan ta tsayar da kukan da take kar ya fito fili, kwata kwata adu.a ta nema ta rasa A hankali take lalube dan samu wajen da zata rabe sai dai me bata san ta kawo kanta waje ba sai da ta lalubo kafar mahaukaci idannuwansa biyu shima yana ta linke ledoji ......... *❣IDAN KA RAINA INDA KAKE❣* Na: *SAJIDA* *_LITATAFAN MARUBUCIYAR_* *_Duk Karyar kada_* *_Yar Mahaukaciya_* *_Neman na kaina_* *_Bani da zabi_* *_Daga tafiya daukar soja_* *_Idan ka raina inda make_* *🌈KAINUWA WRITERS✍🏼 ASSOCIATION*🤝🏻 ```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}``` https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation 5⃣8⃣ *Ina kuke masoya karatun Hausa novels ga dama ta samu domin kuwa kanwar ku 'yar uwar ku ta zo maku da sabon Salon rubutu na zama ni Wanda zata fitar a 1 /1/2020 tare da 'yan uwan ta a cikin zafafa Sha biyar na kainuwa writters insha'allah ga mai son littafin zai biya 200 naira only sunan littafin 'YAN MATAN AMARYA WANDA *MARUBUCIYAR NAN WATAN UMMU HAFEEZ ZATA* *NISHADANTAR* *DAKU A CIKIN SA* *KAR KU BARI* *ABAKU LABARI,* *KARKU MANTA DA* *SUNAN SHI*. *'YAN MATAN AMARYA* *MAISON A SANYA SHI A CIKIN INDA ZAI KARANTA LITTAFIN* 👇🏻 *08168116419* *A wannan number zaku turo Kati ko ta hanyar bank @ AISHA AHMAD,JAIZ BANK* 0002997355 *Sai kayi screen shot dinshi ka turo a wancan number dake sama.* *Daku muke alfahri masoyan mu a duk inda kuke.🤝🏼❤* A hankali take son labewa kar ya ankara da ita sai dai ina ta makaro, gashi jingege da shi ga iska irin na hauka Damkar Aisha ya yi ya rike yana kakaba dariyar da gaba daya daren ya amsa har kamar ana taya shi dariyar domin can can can zaka ji an karashe da hehe Yana kallonta ya ce" ke sai yanzu kika dawo daga aiken? Ai kuwa yau sai na yi kujera da ke Kai kawai aisha take jujuyawa domin tunda ta yi arba da shi gabanta ya yanke ya fadi take tunanin ba jini a jikinta, ji take tamkar wani sashe na jikinta baya anfanuwa Janta ya yi da mugun karfi ya zo wajen mainan da yake tsugune ya hankadata ta je tagaga ta ci tuntube da dutse yatsarta baba ta fashe sannan ta je ta gwaru da mainan nan goshinta nan take ta ji wani abu mai dumi dumi yana bin fuskarta wato jini Sama sama take jiyo muryarsa yana fadin" zauna a nan na samo dutsin da zan dora maki na hau, ina andaninki na aike ki ki je yawo? Ya yi gaba yana dube dube wanda hakan ya farkar da Aisha ta toshe bakinta da hannunta ta samu ta sadada a hankali ta bi dayan hannun wato ba inda ya bi ba Gudu take da iya karfinta wanda du sanyin asubar nan da irin yanda take taka duwatsu da yanda jiri ke dibanta na irin jinnin da take zubarwa bai saka ta tsagaita gudun ba har aka fara kiraye kiraye aka sauko daga sallah mutane suka fara cin karo da ita sai dai ta ga an saki hanya dan ta fice domin du wanda ya ganta a tunaninsa ko mahaukaciya ko wata muguwa ce Allah ya toni asirinta aka yi mata irin dukan nan domin dai a wannan lokacin da wuya ka ga mace mai mutunci a irin wannan yannayin gashi ko dan kwali babu a kanta bata da takalmi haka take sheka gudu kawai Ita kanta bata ta mutanen dake rabewa aman da gari ya yi haske takan nan dakata ta huta kafin ta ci gaba da tafiya tana dizgar kuka tamkar ranta ya fita Ta wani layi ta biyo dan ta samu ta karasa da wuri, sai dai nan ta ga abinda ya kara tayar mata da hankali, Tsohon saurayinta ne yusuf ya fitar da mota daga wani mamakeken gida, ya sha babar gari yana kokarin shiga motar shima Allah ya nuna masa ita Kallonta yake yana al.ajabin ita ce kuwa? Yarinyar da ya so tamkar hauka, wada a kofar gidansu ta tofa masa yawu ta ce" ni gaskiya bakai min ba, ka cika naci nace bana sonka? Kai talaka ni talaka shikenan sai mu dawo muna jera talakawan yaya masu zuciya a mace? Kai idan ka kuka tsayar da ni sai nai maka ihun kwarto , banza mahaukaci ni da kai sai dai na baka bara Ta juya masa dara daran idannuwanta ta juya ta shigewarta gidansu wanda sai da ta daga ledar buhu ta shige a matsayin kofar dake kare gidansu Kanta ta sada zuciyarta na dokawa ta ji daman bata biyo layin ba, ji take inama da hali ta juya kawai ta koma sai dai kashhhhh muryarsa ta ji ya ce" Almajira ce ko mahaukaciya da safen nan? Zo ki karbi sadaka baiwar Allah Ya fada yana mai zaro wata sabuwar naira dubu guda daga gaban motarsa yanai mata nuni Kanta ta kara sadawa sumi sumi ta shige domin ba zata iya kallonsa ba, ya sha fama a kanta a lokacin yana karatu kamar ita abin hawa ma wuya yake bashi sai dai ko nawa gare shi burinsa ya bata , sai ta karbe take yi masa korar kare ta fatatake shi Jingina ya yi da mota yana kallonta har ta shige wata kwana Ajiyar zuciya ya sauke a fili ya furta" me ya same ki mai muni haka bugun zuciyata? Can ya ja tsaki ya furta" banza ce ke zuciyar nan tawa, ki rasa abin so sai wada ya danganta ki da kare? Ta je kawai Allah ya sawaka nima na iya da matar da nake aure ehe Ya bude mitarsa ya shige abinsa ya daga domin Abuja ya nufa A wannan rana Aisha bata karaso anguwarsu ba sai da karfe goma sha daya ta yi, tafiyar kafa ne ta sha har can, idan ka ganta dole ka ajiyeta a dayan biyu ta haukace ne ko tana kan hanya Sannan a wannan lokacin du wata majalisa ta anguwar, du wasu masu zaman kawai du wasu yan mata masu zaman kofar gida, du wasu yara masu bin mahaukata suna tsokana sun yi cccccaaaaa sun cika anguwar kowa yana abinda ya fi kwarewa ana ta labarai ana iya shege So take ta shige ba tare da an ganeta ba sai dai ina, tunda rabe mai man ja ya ganeta ya fito ya daga murya ya ce" jama a me nake ganni ne nan tamkar matar gwomna? Kai dadina da bariki har ta jefo ki ? Yara maza da yan mata kai harda matan auren mararsa aikin yi suka aniya bin bayan Aisha suna tofa mata mugayen kalaman da idan da ne sai ta tsire su sannan ta take su ta fice, aman a yau kanta a kasa, kunya take ji ta rayuwa, mamaki take na abinda duniya ta yi mata tun ba.a je ko.ina ba, mamaki take na yanda mutanen duniya suka fasarata, su tunanin su ta je yawon bariki kennan? So take ta juya ta roke su , su ji kanta su barta ta yi tafiyarta sai dai jinsu take tamkar sirikanta ta kasa hada ido da su tamkar ta yi masu karya, nauyinsu take ji fiye da girman kanta Bata gama mamaki ba sai da ta ga raliya ta yi wani irin dirowa gabanta, ai kuwa du ake kallon su , Raliya ta juya kananuwan idannuwanta ta ce" ke mai kyau , gashi, fari ko? To yau ni mumuna na kwace maki saurayin naki wanda yake kashe maki kudi auren har sauran kwana hudu! Toh idan ma labarin auren kika ji kika zo ki wargaza min farin ciki karya kike, idan takamarki sauko wani a can ya kwana fahad ba zai zauna da yar bariki sauran karti ba Tana fada tana kada jikinta , jira take kadan Aisha ta furta wani abu ta nuna mata itama fa ta fantsamo barikin ta iya tas sai ta dameta ta shanye, a da ne take binta tanai mata fadanci ko dan a anguwa a ringa kallonta a babar yarinya tana kawance da Aisha wace du yawancin samarin anguwar ke sonta, a haka ne ta yi sayrayi fahad, yana kashewa Aisha kudi sai dai a kulun tana nuna masa itafa ba zata iya abinda yake so ba wato a more a titi, du mugun halayen Aisha abinda bata saka kanta a ciki ba kennan, mugun halinta ita kawai lashe mony ce, hakan ya sa Fahad ya janye domin shi daman abinda ya kawo shi kennan, Raliya na gannin hakan ta fara bin fahad du inda ta san zata same shi, bayan barin aisha gida ne Fahad ya amaince mata aman da sharatsin sai ya santa a ya mace daga baya zai aureta Da yake idannuwanta sun rufe ta amince masa suke kebancewa ba tare da ta kiya masa ba , a haukanta da gaske auren nata zai yi bayan ya gama wanketa da karyar cewa zai je ya zo da iyayensa da kudin aure da komai dan haka su shiga shirye shirye sai ya dawo daga Kd Aisha ta sada kanta bata iya cewa Raliya komai ba tana son zagayeta ta fice Raliya ta janyo hannunta da dan karfi Wani saurayi mai suna Musa ya ce" ke ralos baki da hankali ne? Bakya tsoron cutar S? Kinga fa jini take zubarwa ki je ki kwasa? Ai da sauri ta bata gu, jin hakan ya saka sauran ma suka sakar mata hanya ta ci gaba da tafiya kirjinta na wani irin dokawa ta nufi gidansu da dumbin tashin hankalin me zata cewa iyayenta? Me zata ce masu? A irin yanda ta fice ta bar su idan ta koma yanzu ta kale su a yaya? Daman gidansu shi ne aljanarta? Gaban iyayenta koda a cikin akurki ne nan ne konciyar hankalinta? Tana tunkarar gidan ta fara hango wani tashin hankalin, ba gidansu ba labarin gidansu sai wani shago da take gani a madadin gidansu, Ido ta murza da dan karfi ta zabura ta waigo bayanta manyan dun sun gudu gudun kar ta goga masu cuta sai yan tsiraku yaran da basa jin maganar iyayensu sunna biye da ita sunai mata wakar mahaukaciya yar macukule Da sauri ta ji wani karfi ya zo mata ta karasa wajen kanta ta rike ragar ta ce" kai kai malan, ina suke? Ina iyayena suke? Ina mamana? Ina abanna? Wayo na shiga uku, wayo ni Aisha kaicon rayuwana, ina iyayena suke , ina suka shiga? Ina zan gansu? Ya Allah kar ka sa na yi mugun ji, ya Allah ka sa iyayena na nan a raye, ya Allah ka farkar da ni a wannan dogon mafarkin na gannin da kanwata mun fito a makaranta , ta Allah Ta fashe da kuka ta duke a jikin ragar da aka mugun kayatata an zuba kayan abinci na zamani na talakawa da masu hannu da shuni, da ma.aikata yan yara suna ta kulawa da wasu datijai biyu maza wa.inda tunda Aisha ta karaso suke kallonta, dayan ya juya da sauri ya kalli datijo daya wanda ke sanye da kayan mu na hausa ya yi kyau abinsa da gemunsa da carbinsa a hannu da alama shi ne mai wajen Da sauri mutumin ya kara juyowa ya kali mutumin ya kuma kalli aisha dake ta magangannu hannayenta bibiyu a saman kanta fadi take mamana Abanna *❣IDAN KA RAINA INDA KAKE❣* Na: *SAJIDA* *_LITATAFAN MARUBUCIYAR_* *_Duk Karyar kada_* *_Yar Mahaukaciya_* *_Neman na kaina_* *_Bani da zabi_* *_Daga tafiya daukar soja_* *_Idan ka raina inda make_* *🌈KAINUWA WRITERS✍🏼 ASSOCIATION*🤝🏻 ```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}``` https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation 5⃣9⃣ A razane ya ce" malan wannan ba nana Aisha bace? Malan dake kallon Aisha a tsugune, ya maido dubansa wajen amininsa malan tanko, ya kuma duban Aisha, bai iya cewa komai ba sai mikewa da ya samu ya yi gwuiwa a sace ya zo inda take ya dan duka ya kamo hannunta ya ce" tashi ki suturta jikinki ki daina janyowa kanki maganar duniya mana ya Aisha Da wani irin razana ta dago tana dubansa, tsoro da mamaki suka saka ta wangale baki, mikewa ta yi tana kokarin rukunme shi sai dai ya dan baya kadan ya mika mata abinda ke hannunsa wani abin rufa ne dake daya cikin kayan da ake rufe kayan sana.ar idan xata rufe shagon Jiki a sanyaye ta karba ta luluba a jikinta tana mai binsa da kallo aman ta kasa furta ko wace kalma Ta ciki shagon ya shiga ratsawa ana kallonsa ana gaishe shi ana bin wwace ke biye da shi jiki a sanyaye da kallo har suka shige ta wata yar kofa suka bilo ta cikin wani gida Kallon gidan kawai take, gaba daya farar kasa ce a kasa luflufluf Haka suka shige suka tafi har suka karaso wani mamakeken falo Ita dai bata juya ba dan kawai ta sani ne ko me zai zama ba zai bace mata ba a rayuwa, aman tana cike da fargaba Suna shiga ta zaro ido, wanda idannuwanta suka sauka kanta ta danyace ta dawo wata sabuwar yarinya, tana zaune tana faman linki tana fadin" haba malan kai nake jira, ni fa wannan lamarin sai ya saka zuciyata ta mutu da yawa, ka ga yaron nan fir ya hana na mktsa jikina har ciwo yake, wai yanzuma na dauko kayanka na ware masu dati wai yarinyar nan saude ta zaburo na kawo ta wanke, Allah na tuba sai kace ina hauka ne? Ni na baiwa wata aikin mijina? Da kyar malan ta amince ta bar min aikin ladana bayan na yi mata jan ido na nuna mata fa sai na.......... Shiru ta yi gannin yanda malan ya tsaya ya kafeta da ido har idannuwanta suka sauka kan abinda yake son ta ganni Ido ta zaro, gabanta ya bada wani irin dukan da ta ji zata sume dan razana, innalilahi wa.ina ilaihi raj.une, Shine abinda ta furta a lokacin da Aisha ta cire rufar dake kanta ta bayanna a gabn Mama, Gaba daya kafafuwanta ne suka dauki rawa, so take ta karasa wajenta aman ji take tamkar ba ita ba, mamana ce wannan? Abana daman kai ne? Aisha ta furta tana mai rarabe kalmomin tamkar mai koyon magana Mama ce ta ji wani abu ya tsaya mata a zuciya, tsoro ya dirar mata, Aishanta ne haka? Aishanta yarinya yar gayu? Ina ta je haka ya sameta? Wai a haka suna masu binta da adu.a ne? Ya salam Kwalar dake tare a idannuwan Aisha suka samu suka zubo, a hankali ta fara takawa dan karasawa kusan mama sai dai wani abin da ya fadar mata da gaba, abinda maman bata taba yi mata ba du irin fitsarewar da tayi zaman yi mata Wani mugun harara ne mama ta zabgawa Aisha kafin take juyawa wajen Aba da alamun bacin rai ta ce" Malan , me wannan marar godewa Allahn ta dawo yi min? Ko dan ta ga yanzu muna cikin daulan ne ta dawo a ci da ita? Haba malan ya zaka yiwa butulu hanyar dawowa wajen mu? Wannan yarinyar bata san alkhairi ba, sannan ta kasance mai son konta fiye da yan uwanta , kana gani du irin yanda nake tafe da ita nake yiwa dukan muradinta biyaya tamkar itace uwar ni kuwa yar aman irin sakayar da ta yi mana yanzu me ta dawo nema? Malan da ya tsare mama da kallo, irin kallon nan me sakawa ka yi gum da bakinka ne, tun tana zubar da dan karfinta har ta yi shiru ta sada kai tana sheshekar kuka tamkar a lokacin abin ke faruwa da ita take ganni A hankali makan ya taka ya karasa kusa da ita, murya a nitse ya ce" ya Mariama, ya ummu nana Aisha da Rauda, uwar gidan Malan Ahmad, ya dan rage murya ya ce" kai harda amaryama du ke daya Kamar yarinya mama ta dan turo baki ta juya bayanta irin ta ki rarashin Dubansa ya kai wajen Aisha ya ce" ki shiga cikin wancen dakin ki yi salar da baki yi ba Aisha A hankali ta juya bata daina kukan ba ta nufi inda Aba ya nuna mata wani tsoron mama wanda a da bata ji ne ta ji yanzu ya sauko mata Malan ya juya inda ta juya yana dan murmushi ya ce" tunda bakya so ace maki amaryar shikenan zan kawo maki kanwa sai ta taya ki zama Murmushi mama ta yi tana kallonsa bata ce komai ba Malan ya ce " su dai mata lamarinsu sai su, haba maman yara na yi tunanin zaki yi farin ciki ne ki godewa Allah da ya dawo maki da ita da ranta ki yi mata fatan kara shiryuwa? Har kin manta hawayenki na kowani dare kina rokon Allah da ya kare maki yarki? Ko na tuna maki irin yanda zaki dadaba ni cikin talatainin dare ki haske min ido da kwon fitila ki ce" malan ka tashi kawai, ya zaka iya rintsawa bayan bamu san halin da Aisharmu ke ciki ba? Da sauri mama ta sada kanta dan ta ji kunya ainun na abinda yake fada domin da yanayin zolaya ne yake fadar abin Mirmushi ya yi ya kuma dago da kanta ya ce" ki duba ki ga sakayar ubangiji da hakuri inda ya kai mu, mu ne a cikin wannan gida a matsayin malakinmu ga shago wanda kaf anguwarnan nan suke sari a matsayin malakina, harda masu gadin gidan da muke da mota da mai tuka mu, Ina gannin godiya ga Allah shine abinda yafi dacewa da mu sai Allah ya kara yi mana haske a zamantakewarmu Kanta kawai take gyada masa alamar ta gamsu da abinda ya fada....... Tunda ta fara tashin hankalin nan ya tayar da sallar asubahi wanda tunda ta ga fitowarsa daga dakin Rauda take biye da shi tana rusa kuka tana fadan magangannun da ba wani anfani ko ya dawo da agogo baya ba Yana salamewa ya kai dubansa wajen agogo, ya makara a sallah yau shi yasa ya yi abinsa a gida, a hankali ya bude alkur.ani ya kawo bakara ya bude ya shiga karantawa cikin nutsuwa Bata dubi girman karatun nan ba, bata dubi irin lokacin da mijinta ya ware dan kusanta kansa da ubangijinsa ba , ta dage, ta murje idannuwanta tana tayar masa da hankali dan kawai ya kwana a dakin yar uwarta har tana yi masa ikirarin ya ji kunya A hankali ya rufe alkur.anin domin a gaskiya karantawa yake aman du ta tayar masa da hankali baya jinsa yanda yake so Dubansa ya kai kanta, wai tashin hankaline ya sameta du ta tsige acucin dake kanta ta yi firifiri da ita tana ta haikar baki har fadi take ita walahi yarinyar can ta yi kadan ta raba miji da ita, ita ba da ita ba zata yi sai dai ta yi da shi shi Sudais, shi Elhaj sudais, idan an ce ta hadu da shi a titi ne ta gaya masa irin maganar nan yayi imanin ko hada ido da shi ba zata iya ba, aman aure mai daraja ya sa har take iya kallon kwayar idannuwansa ta kafta masa rashin mutunci, kai da ba dan yana so wannan ranar ya wuni cikin farin ba da ya baiwa rashin hankalinta dama ya samu shima ya koya mata hankali ko ta daina tunanin girmansu daya ne Mikewa ya yi ya canza jalabiyar dake jikinsa ya fito da niyar shiga dakin Rauda sai dai me ganninta ya yi a fallo zaune, duda cikin dabara ta dan karkace a zaman kamar ta bada salon zama ne ita kuwa tana kauce azabar da jikinta ke yi mata na radadi, Wani irin fayau ta yi masa a ido, baiwar Allah sai ta dan kanance masa a ido, A hankali ya nufe yana mai oyoyo da kanshinta dake yi masa maraba bai ma lura da Hafsat ba shi dai burinsa ya jingina da ita ya ji batu daga gareta Humaira ce ta biyo bayansa tana girgizar jin masifa ta karaso har fallon ta iso tana taunar cingom ta ce" aikin banza wai ba sabon ba, ke nan har dadin miji kika sani? Yaushema ya aure ki? Ke har kin samu waje kin fito fallo kin hakimce ke ga matar gida ko Da mamaki Sudais ya juyo wajen Humaira zai yi magana sai dai ya ji...... *❣IDAN KA RAINA INDA KAKE❣* Na: *SAJIDA* *_LITATAFAN MARUBUCIYAR_* *_Duk Karyar kada_* *_Yar Mahaukaciya_* *_Neman na kaina_* *_Bani da zabi_* *_Daga tafiya daukar soja_* *_Idan ka raina inda make_* *🌈KAINUWA WRITERS✍🏼 ASSOCIATION*🤝🏻 ```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}``` https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation 6⃣0⃣ A gagauce ........ Hafsat ce ta muke ta ce" sis tashi ki ga mu tafi Da haushi Humaira ta ce" eh man sai ta tashi ku tafi, ku ai dangin miji haka ne , ku raka wannan ku raka wannan, to ni nafi karfinki yarinya banza kawai Sudais ya kama habarsa a ransa ya ayanna ikon Allah, kaucewa nake kara takaloni take yarinyar nan Hafsat ta girgiza kai, da ba fan tana tsoron yayanta ba yau da Humaira ta ga tashen iskanci, yau da ta bambance iskanci koyo da wanda aka iya, sakara da bata iya kishi ba, ita du iliminta du dadewarta a cikin gayu ashe a 0 ne? Kokarin jan hannun Rauda take wace tunda Sudais ya fito ta sada kanta tamkar ba ita ce ta yi iya yinta ta tsala wanka dan su yi tozali da juna ba, bata so kwatakwata ya dauketa a wata raguwa, sai dai wata gungurmemiyar kunyarsa ta hana ta yi ido hudu da shi sai sisine kai take tamkar tana gaban sirikinta, du kuwa irin rashin mutuncin da matarsa ke girbawa sai ta kasa koda kallonta bare ta mayar mata da martani, kai ita bata ma tunanin zata iya tsayuwa ta biyewa wannan matar domin ta lura yar hayaniya ce, idan ta sako abu da tashin hankali ganninta a haka zata cin masa ko menene....... Ido ta rintse ta samu ta mike sai dai ta kasa cirawa ta yi gaba Hafsat da har ta yi gaba ta juyo, cike da jin haushin wai yaya yana jinta aman dan ya daure mata ya kasa tsawatar mata sai shuka iskancinta take son ranta, Humaira ta ce" ba zaki taba fada a wajen mijina ba, domin kuwa koda ya radeki da abubuwa dan wani nufinsa ne, ko ya taba furta maki kalmar so ne? Gaban Rauda ya fadi, idan ba a lokacin da yake sex da ita ba bata ji inda ya furta mata kalmar so ba, ya dai fadi magangannu masu sanyayar da zuciya irin inda ya ce da ita" *sai da ita rayuwarsa*, aman ai hakan kana iya gayawa mutun ko dan ya kontar da hankalinsa a kanka, So take ta kawar da tunanika irin haka sai dai abinda da zuga, shedan ne ko meye ita dai wani abu na ingizata, fadi mata yake" hakane man, wannan ita kadai yake iya so, ba gashi ba tana fadar abubuwan nan ya kasa magana, ba gashi ba tana zage zage tana yayabawa kowa magana aman ya kasa tsawatar mata? Gata dai tsaye tana fadin komai ya kasa cewa ba haka bane Shikenan ta saki jiki har ya kaita irin wannan wajen ? Da wani kallo ta dago ta sauke idannuwanta saman kansa, Ita yake kallo da tsumamun idannuwansa, a hankali ya tako inda ta ja ta tsayan nan ta kasa cirawa ya rike hannunta na dama Abinka da muryar sudais bata da sirri sai dai kawai idan yayi magana a wajen da ba za.a ji ba....ya ce" da zafi har yanzu ko? Rauda ta yi luuu da idonta da take ji yanai mata nauyi dan tsabar haushinsa take ji, aa ba zafi da yake ba mutun bace ni Ta fada a ranta aman a fili fuskarta ya nuna da cikin ranta a bace yake sosai A hankali take kokarin kwace hannunta daga cikin nasa shi kuwa yana kara rikewa so yake ya taimaka mata ya kaita dakin aman ina ran Rauda ya gama baci bata san lokacin da ta ce" ka cikani Malan ka cika ni! Ka cika ni nace, ka kama hannun matar so ba ni ba, ni ba zan iya zama a wajen da ba.a sona ba! Wly ba za.a kasheni da yarintata ba na zauna ana yi min gori kulun kwannan duniya gidanmu zan je Ke ki je din! Sudais ya fada cikin karaji da daga murya wanda ya saka gaba dayansu sukai shiru suna kallonsa Cika hannunta ya yi ya nunota da yatsa ya ce" idan kin bar ni sai me? Idan kin yi nisa da ni sai me? Hakuri zan yi, na iya rayuwa ba ke Rauda, Har sau nawa zan nuna maki irin tarin son da nake maki ya fi karfin na kamanta shi da yayatu na baki sai dai na aikata shi ki karance shi a aikina zuwa gareki? A tare suke kallonsa, Rauda na yi masa kallo mai cike da soyaya, Hafsat na yi masa kallon shikennan yau ya fada hankali zai konta tana mai matsanancin jin dadi, Humaira na yi masa kallon tsoro, tsoro ya dirar mata, yana sonta? Har yake iya fada a bainar nasi du irin girman kansa da nauyin bakinsa? Sudais ya ci gaba da magana jiki a mace ya ce" ki daina anfani da damar da Allah ya baki kina rikita min lisafi MATA, ki daina abu irin na kananuwan yara mana........ Mata na fada *ina son ki , ina son ki, ina son ki* shikenan na fada kuma za.ina fada maki kulun kin ji? Sai ki yi kokari ki damki damar nan ki bani wahala Yana gama fada ya juya bai bi ta kan kowace ba ya fice ya nufi gidansu wajen momy Humaira dake tsaye ta bi bayansa da kallo kirjinta na mugun doka mata Faduwar gaban nan da ba.a so ne ta sameta ta cira da niyar shako wuyan Rauda ta kasheta ta huta sai dai ji kake dim ta kai kasa sumamiya Da Rauda da Hafsat a tare suka kalli junna kafin cikin tashin hankali suke nufarta Rauda ce ta fara juyota ta ga filat ta tafi , hannu ta dora saman kanta tana kallon Hafsat ta ce" na shiga ukuna Hafsat ta mutu fa Hafsat ta zaro ido ta nufi wajen waya da gudu dan kira.... Tana samun yayanta cikin tashin hankali shima ya bada umarnin kar su tabata gayannan Kaiwa kaiwa suka yi shi da docter Amina wada tana zuwa ta nufi Humaira ta shiga gannin ta aunata Dago fa kanta ta yi ta ce" bata mutu ba, ku kama min ita Sudais kadai ya cicibeta ya sakata a mota aman su Rauda suna ji suna ganni yace su zauna ba zasu je ba Haka suka kai Humaira asibiti wace kuma wani tashin hankalin jini take zubarwa ta kasanta Ana zuwa aka shige da ita bayan docter amina ta bada tabacin faduwa kawai ta yi aka shiga baiwa Humaita taimakon gagawa Sun jima cikin dakin kafin suke fitowa Docter Amina ce ta kirayi Sudais office dinta Suna shiga ya zauna hankalinsa du a tashe ya dafe goshinsa yana kallon docter Amina Ajiyar zuciya ta sauke ta ce" elhaj, jininta ya hau sosai, sannan sanadiyar faduwar da ta yi kan cikinta dan karamin cikin dake jikinta na sati hudu ya zube domin mun yi iya yin mu aman bamu samu mun tsayar da shi ba Da tashin hankali Sudais ke kallonta, ciki? Ya furta yana kallonta Docter Amina ta ce" eh haka ciki, ka yi hakuri Allah ya bata lafiya ya maye gurbi da mai zama Bai iya bata amsa ba sai mikewa ya yi ya nufi dakin da Humaira ke konce Yana shiga ya tarar barci take, a hankali ya zauna ya tsura mata ido, Me yayi zafi haka Humaira? Gashi Allah ya bani abinda nake neman ido rufe aman ya tafi? Ido ya lumshe ya furta astagfrullah, yayi imanin wannan cikin koda ba.a yi haka ba ba mai zama bane zai yi tafiyarsa ne aman sosai ya ji abin a ransa Farkawa Humaira ta yi da kuka, ta kai dubanta wajen sudais tanai masa kallon tsana A fili ta furta" ni kake cewa wata kana so a gabana Sudais? Saidais ya mike ya karasa wajenta da sauri ya dafa hannunta ya ce" ki yi hakuri humaira kar ki kuma dagawa kanki hankali kin ji? Kin ga sanadiyar wannan tashin hankalin har mun yi asarar babynmu ki nutsu kin ji? Humaira ta yatsina fuska, dan ta kara masa haushi ta kasa dane abinda ke ranta ta ce" ai ji daman ba haihuwar nake so ba a hakama kana wulakanta ni ina da na haihu ja tsufa? Da wani irin mamaki yake dubanta, kafin ya ji du wani tausayinta da yake ji ya fice masa a rai Mikewa ya yi ya fice a dakin ya je ya bayar da carte dinsa aka yi regler komai na harkar rashin lafiyar ya shiga motarsa ya tayar ya koma gidansa Yana zuwa dakinsa ya shiga Ya jima yana nazari tabas hakan shine ta dace da shi dan haka ya mike ya shirya cikin shigar kamala ya fice a gidan ba tare da ya nemi kowace a cikinsu ba Bai zame ko.ina ba sai wajen alwalin Humaira....... 😌 *❣IDAN KA RAINA INDA KAKE❣* Na: *SAJIDA* *_LITATAFAN MARUBUCIYAR_* *_Duk Karyar kada_* *_Yar Mahaukaciya_* *_Neman na kaina_* *_Bani da zabi_* *_Daga tafiya daukar soja_* *_Idan ka raina inda make_* *🌈KAINUWA WRITERS✍🏼 ASSOCIATION*🤝🏻 ```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}``` https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation 6⃣1⃣ *tsaraba* Ki samu gyadar miyarki kwaya goma idan yin farko.ne, ki dake su lufluf ki dafa kwai kwaya biyu ki yanyanka a ciki ki samu lafiyayiyar zumuwarki ki hada ki cakule yayi tamkar kwado ki cinye ki side kwannonki idan lokaci yayi ki je turaka kawai! 😉🙃😇 sai kice Allah ya sakawa ummu lalla da alkhairi🙈 Tunda ya fara magana cikin nutsuwa da zaro kalamai malan Ahmadu ke girgiza kai yana tir yana mamaki yana tunanin du yanda ake ciki iyayenta basu san da haka ba, Kunyar Elhaj Sudais ce ya ji ta rufe shi, ya rasa ta ina zai fara har gashi mai aukuwa ta auku wato ya yanke hukuncin da dole a dube shi tunda sai da yayi dogon nazari Cike da kunya Malan ahmadu ya ce " ka yi mutunci, ka yi kawaici, ka yi hakuri, ka nuna fushi aman da alama yarinya hata san inda aka nufa ba, na yi mamaki, na ji kunya da jin wannan lamari da wai AISHA HUMAIRA ke aikatawa a gidan miji, Shin iyayenta basa nusar da ita ne ko kunnen kashi ne da ita? Ban san ta ina zan faro baka hakuri ba Elhaj sai dai nace ka san yayan yanzu ka haife su ne baka haifi halinsu ba Ka yi hakuri kuma za.a yi yanda kace din in sha Allah Shima yana matukar jin kunyar datijon domin ya san mutunci , bai so ba kwatakwata bai so ba ta kai su ga haka da ita aman sai da ta kai shi bango, mijinta ai ba tsaranta bane....ko a shekarar haihuwa ya tabata ya bata mai yawa aman sai tana yin tafiyar rayuwarsu tamkar bata cikin musulmai ma bale a yi maganar musulma? Bai iya kara komai daga haka ba ya mike ya yiwa malan Ahmadu alkhairi na mamaki kafin yake juyawa gwuiwa sace ya bar gidan ya kama hanyar ma.aikatarsa ......... Yana son zuwa ya daidaita wasu lamuran ne Tunda ya je yake aiki, bai samu ya tsaya ba sai da ya tabatar ya daidaita komai yanda yake so ya kwashi wasu takardu ya rufe office din ya fito ya shiga mota suka yi da samir su hadu gida Bai zame ko.ina ba sai aeroport ya je yayi abinda ya yi ya karasa gida Yana zuwa bai neme su ba ya tsaya da samir suka gama tataunawa kafin yake tafiya shima ya shige gida Dakinsa ya je ya konta ya rufe ya kashe komai yayi tsai da ransa Wayoyinsa ke kuka tunda ya fice ya kai dubansa gannin momy ce kira ba adadi da maman humaira wanda yayi imanin humairan ne ke kiransa da wayarta , Kiran na momy ya daga ya yi salama Momy ta amsa cike da datako ta ce " uban masu gida haka aka yi kuma? Sudais ya yi tsam kafin yake cewa" hakan shine daidai Momyna Momy ta gyada kai, zata yi masa magana aman sai ya sauko domin bai iya fushi ba bata so ta tirsasa shi a yi abinda bai dace ba, Nan yayi mata doguwar salamar da ta sha mamaki ta yarda lale fa ya dauki abin da zafi da yawa Karfe takwas na dare suna zaune a falon Rauda suna cin crepe haka da chocolate ya shigo dakin Kokarin mikewa Hafsat ke yi ya ce" ki tsaya dauko mata abinda zata bukata na hanya kawai sai ki je Samir ya kai ki gida Da mamaki Hafsat ta amsa da toh aman bata tsaya wani tambaye tambaye ba domin fuskarsa bata bata damar hakan ba Rauda kuwa tsai ta yi tana mai kallonsa, so take su hada ido aman bai yarda ba, ransa a bace sai ta ji wani irin sanyi sanyi na ratsata tamkar bata da lafiya A hankali ta mike da nufin nufarsa aman sai ya shigeta ya barta nan tsaye ya yi wajen kayanta Dogon wando ne da 4iga a jikinta dan haka sai ya dauko mata wani hijab zurkubebe mai nauyin gaske mai ruwan blue ya zo daidai inda take tsaye ya saka mata ya kama hannunta inda Hafsat ta bi bayansu da yar jakar hannu Wata motar ce baka suka shige baya su Hafsat shi kuwa ya bude gidan gaba ya shiga Rauda gumm kake ji ta afka tunani, tsoro take ina zasu? Karde a je yayi fushi zai mayar da ita gida ne?🤦‍♀ Basu zame ko.ina ba sai aeroport yana yi yana duba lokaci sauran yan mintuna jirginsu ya tashi Bai wani yi doguwan ban kwana da Samir ba suka fice yana rike da hannun Rauda wace ke raraba ido tana kallon cikin aeroport din tamkar an sakota sabuwar duniya Haka suka je aka shigar da yar jakar hannunta da wayoyinsa kafin yake shiga ya je da passport dinsa amininsa ya jashi su je sukai shige da fice aka samawa Rauda tiketin tafiya domin abin na manya ne suka fito ya tarar da uta nan inda ake jiran jirgin Zama ya yi ya tsura mata ido, ya tabata tanada tambayoyi sai dai baya so, baya jin zai iya amsata a wannan lokacin, bukatarsa ya samu kulawa kawai Basu kara minti ashirin a zaunen nan ba dad ya zo suka kebe da Sudais suna zantawa wanda Rauda hangensu kawai take Dady sai dan magana yake yana dan girgiza hannun Sudais kafin suke yin salama ya juya Nan aka shiga haramar tafiya inda suka je wajen da za.a tafi da su............ Tafiyar awa shida ne suka yi, suka sauka a kasar Suna fitowa Rauda ta shiga raraba idannu daman bata gama rabuwa da firgitar wai ita ta shiga jirgi ba sai gata an diro da ita a wata kasa ta daban Hannunta ta saka ta damko na Sudais da yake tafiyarsa tamkar kasarsa yana abubuwansa da kuzari A hankali ya kallota ya ga du a firgice take, tausayinta ya ji ya darsun masa inda ya jawota da kyau jikinsa ya nuna mata wani tafkeken abu dake walwali an rubuta *DUBAI* a hankali take ajiyar zuciya ta samu ta dora kanta saman kirjinsa a haka har ya fice ya je wajen reception ya bayar da takardarsa aka yi enregistrer aka bashi kys din motarsa da ya bari a nan Ya fito ya baiwa daya daga cikin yaran dake fitar da motocin ya je ya fitar masa da ita fes da ita domin kulawa ake basu sosai da sosai Sai da ya zagaya ya bude ya saka Rauda gidan gaba kafin yake zagayowa ya shige shima ya tayar da bisimillah ya dauki hanyar mai cike da tsaro ya nufi gidansa dake garin Rauda kam bata samu bakin magana ba sai da ta ganta a wani tafkeken daki, wanda suna shiga Sudais ya cikata ya zarce wajen bed din ya yi bismillah ya fada a reran tamkar yaro yana mai kai hannayensa ya yaye hiramin dake kansa yana cusa yatsusansa cikin yalwatacen gashin kansa yana lumshe ido alamar ya gaji , kuma yana tare da damuwa Baki Rauda ta shagwabe tana kallonsa, ita gaba daya tsoron garia take, ita tsoron komai take .......mama take so, wly aba take so Cike da sangarta ta karasa ta zauna bakin bed din tana dan jan yatsuntsansa ta cuno baki tana ta yi batai magana ba Sudais da ya samu ya dan kallota ya girgiza kai, a ransa ya kara ayannawa yaro , A fili murya can kasa ya ce" kulawa ake da yannayin miji ....koda kana da uzurinka sai ka ajiye daga baya ka bayanna Mata........ Kai ni dai zuciyata a gaskiya a gaskiya batai min adalci ba ehe, bata gannin du abubuwan dake gabanna? Ta tashi ta wani fada kan yar yarinya zaman aurenma sai na koya mata da alama Rauda ta zaro ido ta mike tana kama kugunta ta ce" me me me? Ni ce yarinyar,,,????? Sudais dake kallonta ta kasan ido a ransa ya ayanna ta wani fannin ba, aman a fili ya ce" eh sosai yarinya karama ki wani zo ki dameni da tabetaben kafa yanzu kuma idan nace zan tabaki nima ki bare min baki kina janyo min hadisai wai na sowa dan uwanna abinfa nake sowa kaina kinai min wa.azi na ji tausayinki , to ki kuma tabani ki ga yanda zan sakaki ihu a garinnan Da wani irin kunya Rauda ta juya sumiii sumiii domin yana maimaita abubuwan da ta fada ne a jiya daidai tana c8kin azabar nan Wajen da take tunanin bayi ne ta fada tana mai jin gajiya tana murmushi kasa kasa kafin a fili ta furta "ina son ka sosai SIRE😉 *❣IDAN KA RAINA INDA KAKE❣* Na: *SAJIDA* *_LITATAFAN MARUBUCIYAR_* *_Duk Karyar kada_* *_Yar Mahaukaciya_* *_Neman na kaina_* *_Bani da zabi_* *_Daga tafiya daukar soja_* *_Idan ka raina inda make_* *🌈KAINUWA WRITERS✍🏼 ASSOCIATION*🤝🏻 ```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}``` https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation 6⃣2⃣ Tana fitowa daga wanka cikin sanda ta zo kusan wata farar riga shar shar da ita wace ta san ita ya ajiyema sannan baya dakin Dauka ta yi ta saka cikin gagawa kafin take hayewa saman bed din ba tare da ta shafa komai ba domin bata gani ba Can cikin bacinta take jin yamyamyam jikinta na yi , A hankali ta saka hannunta dan kwabe abinda ke bin fatarta domin a baci take jin lalausan abu na bin jikinta Jin hannunta ta yi ya lume cikin gashi, da sauri ta bude idonta kirjinta na dokawa A hankali ta furta" wayo Allahna, da zafi kar ka yi min plz sire Sudais dake ta fama ya samu ya dan dago, a hankali ya karaso ya rungumeta tsam a jikinsa, Muryarsa har ta canza kala domin daman a kame yake ya ce" ki yarje min MATA Rauda ta dan girgiza kai ta ce" da zafi *mijina*....... tana fadi ne tana cusa fuskarta a kirjinsa Wani irin yar ya ji da wani abu marar musaltuwa, a hankali yake kokarin dago fuskarta har ya samu ya dago ya kafeta da kallo, can ya ce " sai na ji kamar kin kirani da mijinki....kenan kin yarda da hakan? Rauda ta sakar masa murmushi kafin take tataro du wani karfinta ta ce" *mijina*, sannan kuma.. Ta dan yi shiru kafin take saka idannuwanta cikin nasa dar dan ya yarda da abinda,take fada ta ce" *rayuwana, haskena, ruhina ......SOYAYATA* Yanda magangannunta ke fita dala dala haka su ke sukansa daya bayan dayan tun daga zuciyarsa har zuwa gangar jikinsa, gaba daya jikinsa ya mutu...jin kansa yake a wata duniya, wani farin ciki marar misaltuwa yake ji, *Kina so na?* Ya tsinci bakinsa na fadi tamkar sangartacen yaro still idannuwansa na sarke da junna A hankali Rauda ta ce" *INA SON KA* Wani wawan riko ya kara yi mata, muryarsa a rikice ya ce" *MAIMAITA , KI MAIMAITA MIN KHALB, KI YI TA FADA MIN NA ROKE KI* rauda da hawayen farin cikin irin lokacin nan da ta tsinci kanta a ciki ya wanke mata fuska da tsantsar kaunar mijinta da tausayinsa ya sa ta kurumce, ta manta halin da ta shiga a jiya.......ita mai tirr da mata kan wannan lamari sai gata ta yi kundunbala ta kaiwa leben sire sauka da nata, bata tsaya nan ba ta shiga aika masa da sakwonnin da bata san malamin da ya zaunar da ita ya karantar da ita ba sai ganinta ta yi tsundum a harkar tana bada hima To ya maje zuwa biki bale sarki yayi gaya? SIRE ya tsinci kansa a halin zuru.....ya kasance yayi zuru, ya zama marar wayo sai a jikin yar karamar yarinyar matarsa....Raudansa ta diro masa a lokacin da ya cire tsanmanin da lamarin mata, ta shayar da shi mamaki, ta saka shi farin ciki a lokacin da ya nema ya nema ya nema ya rasa, kai Allah amin Allah ya dawamar da shi da Raudansa , Rauda Kamshi santsi, Rauda dandano🙈 haka santin Sire ya kasance inda Rauda ta kuma jin jiki domin wannan karonma komai da zafi zafi yake zuwa, 😟 Dan karamin Hauka ne take zuba masu a asibiti tunda ta buda idannuwanta ta ga mahaifiyarta mahaifinta a zazaune sun yi zugum Tambayar da ta fara jefo masu itace" ina Elhaj kuwa Wani sakaran kallo uwar ta watsa mata kafin ta ce" yana inda kika aike shi AISHA Humaira! Yau dai kin samu abinda kike neme, yau dai kin yi kokari wasan naki yayi armashi.....kin kai shi bango Humaira sai ki warke a salame mu mu fice gida mu je ki rungumi ubanda zaki runguma Da kallon Rashin fahimta take bin mamanta da shi, Kafin ta juya wajen mahaifinta, Kai ya kawar shima haushinta yake ji aunun, ya kali matarsa ya ce" ki bari mana har mu je gida Ra kallo shi ta ce" ka bar ni na haifar da bakin ciki Elhaj, ita a nan har ji take ta shanye shi sai yanda ta yi da shi ko me? Yarinyar nan kwakwaluwar kifi ne da ita, banza ce wawuya ce bata san ruwan dake wankarta ba Mama, pls ki tsaya, me kike nufi da magangannunki ne? Ni na kasa fahimta Humaira ta fada tana kokarin tashi daga koncen tana faman janye abin karin ruwan da aka saka mata Mama ta ce kai tsaye" ina nufin hankalinki ya konta, ya koroki gida sakamakon rashin hankalin da kike toya masa, ya gaji domin ba tare aka halice ku ba, ya gaji da tabara da hauka dan kuwa ba haihuwarsa kikai ba, yace ki je gidanku Wani ihu humaira ta saka ta cire karin ruwan ta dora hannayenta saman kanta, a fili ta furta" na shiga ukuna na lalace, kaji sharin kishiya...du zaman nan da mukai da Elhaj bai fadi haka ba sai yanzu da ya yi aure? Ni Elhaj ya kora? Yana nufin ya sakeni ko me? Walahi bai isa ba walahi sai ya mayar da ni dakina Abanta ne ya matsa ya daga hannu ya bige bakinta ya ce" kul ki yi min shiru sakarya, ke yanzu har kina da kunya da bakin magana? To tashi tunda na ga halama lafitarki kalau sangarta ce ta masu kudi, fice mu je gidan banza ki ci kaniyarki......mu je ki tarar da dakin da babu ac ba luntsumemiyar shinfida Ba cima irin na kasar waje, ba motoci... rayuwa zaki irin ta kowa ba wai ta matar Elhaj Sudais ba, Humaira dole ki yi aikin gida kuma ki ajiye shafe shafe koda zaki yi hauka ne Kamar sakara baki bude take kallon yanda abanta ke hankadata, ta bani kennan dai Sudais ya fadi komai? Ya salam Du laifinsa da bai yi mata dukan mutuwa har ta sare da duniya ba Elhaj, na sha fada mata ba ita ba mu kanmu da Allah muka dogara ya bamu bango Mijinta, aman maimakum ko dan alkhairin da yake yi mana a rayuwa idan bata dauki darajar kalmar miji ba ai ta sasauta wani haukan, ke bakya jin kunyar mahaifiyarsa? Kina dai gani tun mutuncin anguwa daya da muke kawance da ita, Allah ya daukaka yaronta ta jajirce sai da ya aure ki, ke kanki Humaira kin san ba kalarsa bace, kunya da biyaya ya yiwa iyayensa aman ke gaki katuwar banza kin kasa yi mana biyaya, ba komai na ga halamar *Raina inda kike ki kai,* sai mu je gidan ki ci abinda muke ci, kuma indai ni na haife ki ni Baraka daga yau na raba ki da du wata kawa, idan kika yarda kika kuma biyewa wata kaya gaki ga duniyar nan Da sauri ta kali mamanta, aa , wai ba wanda zai saurareta ne? Sai gasata suke ba wanda zai rabeta ta ji sanyi ne? Mijinta, abin alfaharinta, abin takamarta, tinkahonta karyarta du shi ne, gashi du uban dukiyar sa yake bata kawaye na zugata tana siyarwa a ci banza a ci wofi a sayi man shafe shafe masu tsadar balaki a saka atach na karshen kudi a yi mak up na hauka a baza turare du dan a nunawa kawa an fita, yau bata da komai idan Sudais ya saketa ya zatai? Kuka ta fashe da shi lokacin da suka shiga yar karamar motar Aba ya tayar ya halba bakin titi Tana kuka ta ce" haba abanna , ku tausaya min mana, kun ga fa bari na yi Aba bai san lokacin da ya ce" aa ubanki ki kai Humaira, mutuniyar banza ai ke kin yi sa.a da bai fito da hanjin cikin gaba daya kowa ya huta ba, sai me dan kin yi bari? Shima dan Allah ne ya rufa masa asiri bai taka kasa a matsayin danki kina aikata haka ba, ke bara ki ji Allah ya kaimu gidan nan lafiya zan ga ni da ke wa ya fi iya tsageranci idan baki tuba kin natsu dan Allah ba zaki tuba dan ubanki ne! Gumm ta yi tana kifkifta ido, ita bata da waya a hannunta da ta kiraye shi ko.ina yake ta je ta bashi hakuri, yanzu haka zata shiga gidansu ma.aikata da take yiwa dagin kai ita matar elhaj su ganta a haka? Ina ba zai yiwu ba ko ka sake ni sai ka yi hakuri mun yi zaman mu Wanki take tana ta zufa, kayan abansu ne mama ta fitar irin dangin jalabiyoyi , kaya ne masu shegen kyau domin Aba kam an shiga layin Elhazawa Elhaj Sudais ya tatakura ya wanke sirikan nasa Aba ya sha jalabiyoyi na manyan mutane ya nada hirami mama kuwa ta daura atampa ta gani ta fada ta matan manyan da dinkunnan manyan daraja, ta danyace abinta sai shagali take mata a gidan malan Ahmad🤣 Mama na hira Aisha ne da iya karfinta, da ma.aikata da komai aman sai su sha zamansu abinsu ko su je su yo wani aikin du yan aikace aikace Aisha ne ke yi har malan kan tausaya mata wani lokacin sai mama ta murje idannuwanta ta ce" lokacin da Raudana na yi ita kadai ai itama mutun ce, ni ban ga anfanninta ba idan ba zata aikatu ba haka kawai katuwar budurwa sai dai mu ciyar da ita? Ita ba mijin ta fitar ba ita ba karatun ba ta tsayar da komai? Ai gwara aikatau din Sai malan yayi murmushi kawai ya fice abinsa domin ya tabata Mariama na haka ne dan ta ladaftar da yar tata Aisha na tsaka da shanya aka yi salama Dago kanta ta yi ta sauke kan wata mata da yaro a hannunta da kuma goyo Matar ta duka har kasa ta ce" baiwar Allah aikatau muke nema da yan yaranna mun nema mun nema mun rasa dalilin datin dake jikin mu, ku taimaka ku bamu konce ko ku dauke mu aiki komai kankantar biyan Allah ya saka masa albarka Aisha ta ji wani hawaye ya zubo mata tana kallon matar, ita daya ce dai a tsakar gidan dan haka ta matsa kusa da matar ta ce" baiwar ke kuwa ina gidanki? Ina mahaifin yayanki? Matar ta ki yarda ta dago da kanta, ta ce" mahaifinsu yana kauye abinsa, ni kuwa na ga ba zan iya ba kulun cin tuwon bakar dawa da tsanwar miya shine na dauko kananiwan yayana muka shigo birni dan samun aikatau muma mu murje ba zan iya zaman talauci mai muni irin haka ba Aisha ta sauke ajiyar zuciya tana kallonta, can ta nisa ta ce" ba zan ga laifinki ba, domin ban san wace irin rayuwa kike yi a gidanki ba, rokona da ke shine idan har kin ga da hali ki waiwayi gidanki yar uwata domin duniyar nan girma ne da ita abubuwan cikinta nauyi ne da su, wani idan ka kalla wanin ya fi karfin kallon ka, ki yi kokari ki yi tunani domin zama lafiya ya fi zama dan sarki, Bara na je wajen maman mu idan da hali ta taimaka maki kin ji? Aisha ta fada tana juyawa da niyar shigewa baban falon sai ta dan waigo Idannuwanta ne suka sauka a fuskar matar, gabanta ya yanke ya fadi, ba zata manta fuskarta ba ita ce Wani murmushi matar ta sakarwa Aisha kafin take juyawa ta fice fitt da wani irin sauri Hannaye biyu Aisha ta dora a ka nan ta silale sumamiya.....m 💓 *❣IDAN KA RAINA INDA KAKE❣* Na: *SAJIDA* *_LITATAFAN MARUBUCIYAR_* *_Duk Karyar kada_* *_Yar Mahaukaciya_* *_Neman na kaina_* *_Bani da zabi_* *_Daga tafiya daukar soja_* *_Idan ka raina inda make_* *🌈KAINUWA WRITERS✍🏼 ASSOCIATION*🤝🏻 ```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}``` https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation 6⃣3⃣ Innalilahi wa.ina ilaihi raj.une Shine abinda suke ta maimaitawa bayan malamin da yayi ta yiwa Aisha Rukiya kwana da kwanaki kafin ake samu ta yi magana, da sai dai zuru sai kuma ta yi ta ihu tana nuna waje tana gatannan ta dawo itace itace Mama ta yi saurin matsawa kusan malan, murya kasa kasa ta ce" walahi ina tune da ranar, ta shigo tare da yayanta kwaya biyu ta nemi da mu taimaka mata aman sai Aisha ta wulakantata ta kore ta, bayan ta fita ne Rauda ta kwashi wasu suturunta ta bi matar ni dai ban san ya sukai da ita ba da ta dawo ta jima kagin take cewa mama abin mamaki matar nan sunana ta kira , ni kuwa nace da ita to ai ba mamaki domin tana fita a waje ma sai ta ji sunanki da haka muka ci gaba da shagulgulan gabanmu Da kyar aka samu ta barta bayan ta maimaita ba wani nisa zatai ba domin irin masu halayan Aisha take nema dan ita jininsu ne abincinta Daga wannan ranar Aisha ta kuma dawowa wata shiru shiru da ita sosai, bata yawan magana, sannan abu kadan sai ka ga tana hawaye ko ta tsorata, Hakan ya kara tayarwa da mama hankali ta shiga adu.a tana nemawa Aisha sauki wajen Allah Tsohon Saurayin Aisha dai Fahad ne ya dawo yake nacin zuwa wajenta, wani lokacin mama ta fatataketa ta fita wani lokacin ta fashewa mama da kuka wai ita walahi tsoro take ji yana da mata fa, sam ba dan rainin abin hannunsa ba sai dan tsoron matarsa Mama takan ji tausayinta a ranta aman a fili ta nuna ai mai matan shine daidai ita me take tunani? Tana jiran saurayi santali ya fito mata ne? Ai wannan ma Allah ne ya ji kanta ya turo mata da shi dan haka ta karba kawai ta yi hamdallah...... Rayuwar Sudais da Rauda a kasar saudiya Rayuwa ne mai cike da tsari, dumbin kulawa, Rauda na samu wajen mijinta haka shima yana samun tarin soyaya, kulawa, uwa uba nutsuwa a tare da yarinyar da ta yiwa zuciyarsa dirar mikiya sannan ta shayar da shi mamakin yar shila ma mace ce😂 Zaune take ta tsurawa windows ido, filfilfil iskarnan mai dadi mai saka nutsuwa na hurawa, dadin garin manzo ni.ima daga nan ta fito, Hadarin da bai yi shawara ba cida ba komai ne ya fara sakin ruwa, sai garin fiyayaen halita garin gagara gasa garin masoyina 😌, A hankali ta mike ta je ta rufe windows din ta dawo ta zauna zuru da ita Ya jima yana kallonta kafin wayarsa ta dauki ruri ya nufeta Mom shine abinda ya gani dan haka ya daga da salama Bayan sun gaisa Mom ta ce" watanku nawa son ? Ba zaka zo na ganka ba ko? Sudais ya yi murmushi, Mom kennan, wai ya zo ta ganshi, so dai take ya zo ta kara kakaba masa yarinyar nan ya dawo yana ta fama tamakar wani yaro karami kulun bakinsa yana haiga idan ya tarota ta nan sai ta bule ta can Sai da suka gama wayar ya ajiye ya dauki uar karamar ta ma.aikata ya yi kiran wani balarashe imran sukai magana suka gama kafin yake karasowa a hankali wajen Rauda da wata wayar a hannunsa Yana zuwa ya zauna inda ske facing din juna, Yar doguwar riga baka ce a jikinta, gashin kanta ya yi mata luwaiwai sai hannunta na hagu da wani dan abin hannu siriri ta daura shi shikenan sai kanshin da take bazawa Rauda ta zama wata fresh da ita, fatar jikinta ta zama wata mai sulbin gaske sannan ta kara haske, hutu ya bayana ta ko.ina a jikinta koda yaushe cikin gyaran kanta take bata yarda dan sun yi wata biyu da kwana goma sha hudu da shi ba tace wai sun saba, a kulun takan tashi da niyar wannan bakona ne, wanda nake son na birge, na ja ra.ayinsa, na yarda da kalmar tsoka daya ne a miya kowa wawa yake kai masa, dan haka nima ba kowa bace dan ya nuna yana sona ba hakan zai bani damar na zubar da makaman yakin yakar zuciyarsa ba, domin kuwa zama wahe daya ya kori komai, Hakan da ta sakawa ranta ya saka take binsa da dukan matsayinsa na miji a wajenta, tanai masa biyaya ne mudin ranta, sannan tana kokarin bashi hakinsa a duk lokacin da ya nema kai harma kokari take ita kanta ta nema dan ya jita a ransa Tako taka rawa ya yaba harba yayi kari, domin salolinta sun zo masa a yanda yake so, A ranar da cikin baci ya jita tana kai masa hari.....wato tana nuna bukatarta a gare shi , ya ji shi tamkar wani sarki....cike da nustsuwa ya amsa gayatarta harda yayi dare a wajen, tun daga lokacin ya kara sarawa ya sake komai kawai Yar shila ta gama da shi (🤣) Habarta ya saka hannunsa na dama ya dago, kafin yake kashe mata ido daya ya ce" ni wai shashare nin na menene? Bakinta ta turo ta juya masa baya tana dan alamun kuka zatai Juyo da ita yayi, ya shagwabe fuska kamar yanda ta yi ya ce" a sasautawa Sudais yana neman kansa Rauda ta yi walwal da idannuwanta kafin ta ce" sire, a gaskiya ina kishin mijina.....ta ya za.a ce wai ministan wannan gingirmemen garin yana nemawa yarsa aiki a ma.aikatarka sannan a matsayin secretariarka? Aa, ni fa ba yarinya karama bace na san magana idan aka yi, mu koma gida ni gida nake so Ta karashe tana fashewa da kuka bilhaki Ajiyar zuciya ya sauke yana taping din bayanta, har wata zufa ya ji tana karyo masa ta tashin hankali Murya a rine ya ce" ki yi hakuri Mata, yanzu ya kike so a yi? Sasauta rigimar ta yi tana kallonsa ta ce" idan har dole sai ka dauki mace a matsayin secretaria ka dauki matanka aunty da ni mu kasance a kusa da kai Dariya ya fashe mata da shi har yana dan rike ciki kafin yake tsagaitawa ya dan nunota da yatsarsa karama ya ce" ko ku kori du macen da ta zo siyaya wajen mijinku ba, bayan sana.ar dan almajin du yawanci harkar kayan matan ne....shikenan sai mu yi tsawa mu dawo gida abinmu Raudama ta yi murmushi ta fada kirjinsa murya kasa kasa ta ce" koda mijina ya shekara goma a gabannnan a zaune bana tunanin wani zai gane cewar baya aiki domin Allah ya rufa masa asiri fiye da tunaninsa, Farin cikina ina kishin mijina domin ina sonsa Ajiyar zuciya ya sauke ya bata wata runguma mai zafi, A kunnanta itama ya kawo lebensa, a hankali ya ciro harshensa ya lashi gefen kunnen nata, ya kai bakinsa sosai ya ce" kin san meye an fasa daukan nata, sai dai zuciyata ba zata iya harbawa ba in dai tana tunanin kina can waje wajen da wani gardi na iya ganinki, Rauda zan haukace idan na ji labarin kin taba son wani a duniya, zan shiga mugun hali idan na ga wani na kallon min mata........yanzu kuwa duniya ta ki gaskiya, mutane sun lalace......rudin duniya na halakar da bayi, mazonmu ba zai ji dadin wannan lamari ba duda ya san da zuwan zamanin, al.umarsa tana ta manta dumbin alkhairinsa a gareta tana tafka tsiya a doron kasa bayan ta manta wanda ya yita ya fita gannin kanta......ba zan iya barinki ki fita aiki ba, ki yi hakuri Mata Kankame shi ta yi ta shiga kai masa farmaki, yana zuwa da zafi zafinta wanda basu iya tashi sun karasa bed ba sai nan kan lalausan kafet din falon suka baje koli.......🤦‍♀ Haba dady, dan Allah ka yi hakuri ban gansu bane da na hada har su Dady ya watsa mata harara ya juya ya fice abinsa Mahaifiyarta dake zaune tana danna waya ta ce" ke idan kin gama wankin na babanki ki maida hankali ki dora girki mana Mikewa Humaira ta yi tana sharar kwallah ta nufi kayan ta kwashe ta je wajen yin wankin inda mahaifiyarta ta bita da kallo, Gaba daya jikinta ya yi wani tabo tabo Wani wajen tamkar an kona, Fuskarta kuwa ta yi wani mahaukacin baki ta yi mata tsaba tsaba tambar jikin tsaka Humaira dai ta dawo sai kace zarara ita kadai ma magana take idan tana zaune, somin har mafarkin khairath take tsabar ta sakata a ranta fadi take alhakin Khairath da Sudais ne ke binta , khairath bata duniya bale ta yafe mata sudais yana duniyarma aman ta tabata ko tsafi take ba zata iya kai kanta inda yake ba Kuka ne aikinta ba dare ba rana, sai tana susar fatarta tamkar ta yageta ta huta, ta dawo wata kala da ita, abin sai adu.a, takan saka abinci gaba sai ta fashe da kuka, tun bata iya girkawa ba har ta iya wasu abubuwan , aman sam ita bata jin dandannon su a bakinta Sama ta kalla bayan ta gama wankin ta ce" khairath, ina kike? Ke mutuwa kikai........ki godewa allah idan har Allah ya cida ke kin huta, mijinki ne ya wanke ki yana hawaye, cikin nutsuwa ya suturtata ki sannan shi ya raka ki har gidanki na gaskiya, shi ya saka ki yana mai binki a hankali tamkar kwai, yana taisaya maki yana jinki har ransa ya rabu da ke, yana ji yana gani ya dawo ya baro ki a wajen wanda ya halice ki wanda ya fi shi son ki, khairath Allah ya jadada rahama gare ki, ya jikanki Rana gama fada ta fashe da kuka ta duke nan domin wani jiri ne ya kwasheta Mamanta ta mike da sauri ta fada dakin su domin ba zata iya ba, cikin haihuwa ba zai barta ta yi shiru bata lalabi Humaira a wannan yannayin ba Dadynta kuwa murmushi yayi, ya tayar da mota, Dadi yake ji idan ya ga irin haka, yana so ya kara yarda da nutauwarta kafin ya makata islamiya kafin elhajin ya dawo ya je da kansa dan ya ji a matsayin da take idan ya saketa ne sai a yi hakuri a yi fatam samun wani mijin na gari....... Sarah ki daina bina, Sarah bana son ganninki kwata kwata a rayuwa, bana iya buda idannuwanna na gan ki ba tare da na aibata ki ba ki fice sarah Ta karashe tana karajin da ya saka sarah rukunkume jikinta tana kyarma Ta dora hannunta a kai ta rasa inama zata nufa ne? Sarah na dauke da cutar kanjamau, a haka suna cikin wannan tashin hankalin Elhaj ya biyo dare ya rufe dakinta ya afka mata (wa.iyazubillah), har fadi yake dan ubanki da kare kawai bakya yi shima dan baki san ya da zaki yi yayi da ke ba aman ni ubanki ki hana min, ko ki yarda ko na kashe ki na kashe uwarki na bi ta baya sai kun kunbura kun fashe za.a ji warinku mu je mu birne banzaye masu son abin duniya A wannan rana sarah ta ga balaki gannin idannuwanta, daman da yan kuraje dake tsatsafo mata a gabanta wa.inda har wani wari suke tamkar muse haka Abanta ya ringa gugarsu yana darzarsu ya gama da ita ya makawa mahaifiyarta saki yana ikirarin tarbiya ai ta uwa ce dan haka ya saki uwar saki uku sai a je a bi layin karuwanci Tafe dai ne kawai aunty take, aman bata san inda take jefa kafafuwanta ba, zuciyarta ta yi mata nauyi, gidansu suka nufa wanda sai da dan adaidaitar ya ajiye au ya bi su karbo kudinsa Tunda aunty ta shigo ta riko hannun mamanta gam, kallonta take tana hawaye tana tuna irin tarin cutar da ta yiwa iyayenta da kanwarta dan son kanta, kamar yanda bokanta ya fada in dai suka ji sunnan Mama toh zasu tuno da ita ne da muguwar soyayarta a ruhinsu hakan ya sa ta kafe mahaifiyarsu da ido ta ce" ummey, ina MARIAMA take Tamkar bugawar guduma haka sunnan ya shiga kwakwaluwar Ummiey daya bayan daya, wanda a nan ta zube sumamiya............ *❣IDAN KA RAINA INDA KAKE❣* Na: *SAJIDA* *_LITATAFAN MARUBUCIYAR_* *_Duk Karyar kada_* *_Yar Mahaukaciya_* *_Neman na kaina_* *_Bani da zabi_* *_Daga tafiya daukar soja_* *_Idan ka raina inda make_* *🌈KAINUWA WRITERS✍🏼 ASSOCIATION*🤝🏻 ```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}``` https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation 6⃣3⃣ Innalilahi wa.ina ilaihi raj.une Shine abinda suke ta maimaitawa bayan malamin da yayi ta yiwa Aisha Rukiya kwana da kwanaki kafin ake samu ta yi magana, da sai dai zuru sai kuma ta yi ta ihu tana nuna waje tana gatannan ta dawo itace itace Mama ta yi saurin matsawa kusan malan, murya kasa kasa ta ce" walahi ina tune da ranar, ta shigo tare da yayanta kwaya biyu ta nemi da mu taimaka mata aman sai Aisha ta wulakantata ta kore ta, bayan ta fita ne Rauda ta kwashi wasu suturunta ta bi matar ni dai ban san ya sukai da ita ba da ta dawo ta jima kagin take cewa mama abin mamaki matar nan sunana ta kira , ni kuwa nace da ita to ai ba mamaki domin tana fita a waje ma sai ta ji sunanki da haka muka ci gaba da shagulgulan gabanmu Da kyar aka samu ta barta bayan ta maimaita ba wani nisa zatai ba domin irin masu halayan Aisha take nema dan ita jininsu ne abincinta Daga wannan ranar Aisha ta kuma dawowa wata shiru shiru da ita sosai, bata yawan magana, sannan abu kadan sai ka ga tana hawaye ko ta tsorata, Hakan ya kara tayarwa da mama hankali ta shiga adu.a tana nemawa Aisha sauki wajen Allah Tsohon Saurayin Aisha dai Fahad ne ya dawo yake nacin zuwa wajenta, wani lokacin mama ta fatataketa ta fita wani lokacin ta fashewa mama da kuka wai ita walahi tsoro take ji yana da mata fa, sam ba dan rainin abin hannunsa ba sai dan tsoron matarsa Mama takan ji tausayinta a ranta aman a fili ta nuna ai mai matan shine daidai ita me take tunani? Tana jiran saurayi santali ya fito mata ne? Ai wannan ma Allah ne ya ji kanta ya turo mata da shi dan haka ta karba kawai ta yi hamdallah...... Rayuwar Sudais da Rauda a kasar saudiya Rayuwa ne mai cike da tsari, dumbin kulawa, Rauda na samu wajen mijinta haka shima yana samun tarin soyaya, kulawa, uwa uba nutsuwa a tare da yarinyar da ta yiwa zuciyarsa dirar mikiya sannan ta shayar da shi mamakin yar shila ma mace ce😂 Zaune take ta tsurawa windows ido, filfilfil iskarnan mai dadi mai saka nutsuwa na hurawa, dadin garin manzo ni.ima daga nan ta fito, Hadarin da bai yi shawara ba cida ba komai ne ya fara sakin ruwa, sai garin fiyayaen halita garin gagara gasa garin masoyina 😌, A hankali ta mike ta je ta rufe windows din ta dawo ta zauna zuru da ita Ya jima yana kallonta kafin wayarsa ta dauki ruri ya nufeta Mom shine abinda ya gani dan haka ya daga da salama Bayan sun gaisa Mom ta ce" watanku nawa son ? Ba zaka zo na ganka ba ko? Sudais ya yi murmushi, Mom kennan, wai ya zo ta ganshi, so dai take ya zo ta kara kakaba masa yarinyar nan ya dawo yana ta fama tamakar wani yaro karami kulun bakinsa yana haiga idan ya tarota ta nan sai ta bule ta can Sai da suka gama wayar ya ajiye ya dauki uar karamar ta ma.aikata ya yi kiran wani balarashe imran sukai magana suka gama kafin yake karasowa a hankali wajen Rauda da wata wayar a hannunsa Yana zuwa ya zauna inda ske facing din juna, Yar doguwar riga baka ce a jikinta, gashin kanta ya yi mata luwaiwai sai hannunta na hagu da wani dan abin hannu siriri ta daura shi shikenan sai kanshin da take bazawa Rauda ta zama wata fresh da ita, fatar jikinta ta zama wata mai sulbin gaske sannan ta kara haske, hutu ya bayana ta ko.ina a jikinta koda yaushe cikin gyaran kanta take bata yarda dan sun yi wata biyu da kwana goma sha hudu da shi ba tace wai sun saba, a kulun takan tashi da niyar wannan bakona ne, wanda nake son na birge, na ja ra.ayinsa, na yarda da kalmar tsoka daya ne a miya kowa wawa yake kai masa, dan haka nima ba kowa bace dan ya nuna yana sona ba hakan zai bani damar na zubar da makaman yakin yakar zuciyarsa ba, domin kuwa zama wahe daya ya kori komai, Hakan da ta sakawa ranta ya saka take binsa da dukan matsayinsa na miji a wajenta, tanai masa biyaya ne mudin ranta, sannan tana kokarin bashi hakinsa a duk lokacin da ya nema kai harma kokari take ita kanta ta nema dan ya jita a ransa Tako taka rawa ya yaba harba yayi kari, domin salolinta sun zo masa a yanda yake so, A ranar da cikin baci ya jita tana kai masa hari.....wato tana nuna bukatarta a gare shi , ya ji shi tamkar wani sarki....cike da nustsuwa ya amsa gayatarta harda yayi dare a wajen, tun daga lokacin ya kara sarawa ya sake komai kawai Yar shila ta gama da shi (🤣) Habarta ya saka hannunsa na dama ya dago, kafin yake kashe mata ido daya ya ce" ni wai shashare nin na menene? Bakinta ta turo ta juya masa baya tana dan alamun kuka zatai Juyo da ita yayi, ya shagwabe fuska kamar yanda ta yi ya ce" a sasautawa Sudais yana neman kansa Rauda ta yi walwal da idannuwanta kafin ta ce" sire, a gaskiya ina kishin mijina.....ta ya za.a ce wai ministan wannan gingirmemen garin yana nemawa yarsa aiki a ma.aikatarka sannan a matsayin secretariarka? Aa, ni fa ba yarinya karama bace na san magana idan aka yi, mu koma gida ni gida nake so Ta karashe tana fashewa da kuka bilhaki Ajiyar zuciya ya sauke yana taping din bayanta, har wata zufa ya ji tana karyo masa ta tashin hankali Murya a rine ya ce" ki yi hakuri Mata, yanzu ya kike so a yi? Sasauta rigimar ta yi tana kallonsa ta ce" idan har dole sai ka dauki mace a matsayin secretaria ka dauki matanka aunty da ni mu kasance a kusa da kai Dariya ya fashe mata da shi har yana dan rike ciki kafin yake tsagaitawa ya dan nunota da yatsarsa karama ya ce" ko ku kori du macen da ta zo siyaya wajen mijinku ba, bayan sana.ar dan almajin du yawanci harkar kayan matan ne....shikenan sai mu yi tsawa mu dawo gida abinmu Raudama ta yi murmushi ta fada kirjinsa murya kasa kasa ta ce" koda mijina ya shekara goma a gabannnan a zaune bana tunanin wani zai gane cewar baya aiki domin Allah ya rufa masa asiri fiye da tunaninsa, Farin cikina ina kishin mijina domin ina sonsa Ajiyar zuciya ya sauke ya bata wata runguma mai zafi, A kunnanta itama ya kawo lebensa, a hankali ya ciro harshensa ya lashi gefen kunnen nata, ya kai bakinsa sosai ya ce" kin san meye an fasa daukan nata, sai dai zuciyata ba zata iya harbawa ba in dai tana tunanin kina can waje wajen da wani gardi na iya ganinki, Rauda zan haukace idan na ji labarin kin taba son wani a duniya, zan shiga mugun hali idan na ga wani na kallon min mata........yanzu kuwa duniya ta ki gaskiya, mutane sun lalace......rudin duniya na halakar da bayi, mazonmu ba zai ji dadin wannan lamari ba duda ya san da zuwan zamanin, al.umarsa tana ta manta dumbin alkhairinsa a gareta tana tafka tsiya a doron kasa bayan ta manta wanda ya yita ya fita gannin kanta......ba zan iya barinki ki fita aiki ba, ki yi hakuri Mata Kankame shi ta yi ta shiga kai masa farmaki, yana zuwa da zafi zafinta wanda basu iya tashi sun karasa bed ba sai nan kan lalausan kafet din falon suka baje koli.......🤦‍♀ Haba dady, dan Allah ka yi hakuri ban gansu bane da na hada har su Dady ya watsa mata harara ya juya ya fice abinsa Mahaifiyarta dake zaune tana danna waya ta ce" ke idan kin gama wankin na babanki ki maida hankali ki dora girki mana Mikewa Humaira ta yi tana sharar kwallah ta nufi kayan ta kwashe ta je wajen yin wankin inda mahaifiyarta ta bita da kallo, Gaba daya jikinta ya yi wani tabo tabo Wani wajen tamkar an kona, Fuskarta kuwa ta yi wani mahaukacin baki ta yi mata tsaba tsaba tambar jikin tsaka Humaira dai ta dawo sai kace zarara ita kadai ma magana take idan tana zaune, somin har mafarkin khairath take tsabar ta sakata a ranta fadi take alhakin Khairath da Sudais ne ke binta , khairath bata duniya bale ta yafe mata sudais yana duniyarma aman ta tabata ko tsafi take ba zata iya kai kanta inda yake ba Kuka ne aikinta ba dare ba rana, sai tana susar fatarta tamkar ta yageta ta huta, ta dawo wata kala da ita, abin sai adu.a, takan saka abinci gaba sai ta fashe da kuka, tun bata iya girkawa ba har ta iya wasu abubuwan , aman sam ita bata jin dandannon su a bakinta Sama ta kalla bayan ta gama wankin ta ce" khairath, ina kike? Ke mutuwa kikai........ki godewa allah idan har Allah ya cida ke kin huta, mijinki ne ya wanke ki yana hawaye, cikin nutsuwa ya suturtata ki sannan shi ya raka ki har gidanki na gaskiya, shi ya saka ki yana mai binki a hankali tamkar kwai, yana taisaya maki yana jinki har ransa ya rabu da ke, yana ji yana gani ya dawo ya baro ki a wajen wanda ya halice ki wanda ya fi shi son ki, khairath Allah ya jadada rahama gare ki, ya jikanki Rana gama fada ta fashe da kuka ta duke nan domin wani jiri ne ya kwasheta Mamanta ta mike da sauri ta fada dakin su domin ba zata iya ba, cikin haihuwa ba zai barta ta yi shiru bata lalabi Humaira a wannan yannayin ba Dadynta kuwa murmushi yayi, ya tayar da mota, Dadi yake ji idan ya ga irin haka, yana so ya kara yarda da nutauwarta kafin ya makata islamiya kafin elhajin ya dawo ya je da kansa dan ya ji a matsayin da take idan ya saketa ne sai a yi hakuri a yi fatam samun wani mijin na gari....... Sarah ki daina bina, Sarah bana son ganninki kwata kwata a rayuwa, bana iya buda idannuwanna na gan ki ba tare da na aibata ki ba ki fice sarah Ta karashe tana karajin da ya saka sarah rukunkume jikinta tana kyarma Ta dora hannunta a kai ta rasa inama zata nufa ne? Sarah na dauke da cutar kanjamau, a haka suna cikin wannan tashin hankalin Elhaj ya biyo dare ya rufe dakinta ya afka mata (wa.iyazubillah), har fadi yake dan ubanki da kare kawai bakya yi shima dan baki san ya da zaki yi yayi da ke ba aman ni ubanki ki hana min, ko ki yarda ko na kashe ki na kashe uwarki na bi ta baya sai kun kunbura kun fashe za.a ji warinku mu je mu birne banzaye masu son abin duniya A wannan rana sarah ta ga balaki gannin idannuwanta, daman da yan kuraje dake tsatsafo mata a gabanta wa.inda har wani wari suke tamkar muse haka Abanta ya ringa gugarsu yana darzarsu ya gama da ita ya makawa mahaifiyarta saki yana ikirarin tarbiya ai ta uwa ce dan haka ya saki uwar saki uku sai a je a bi layin karuwanci Tafe dai ne kawai aunty take, aman bata san inda take jefa kafafuwanta ba, zuciyarta ta yi mata nauyi, gidansu suka nufa wanda sai da dan adaidaitar ya ajiye au ya bi su karbo kudinsa Tunda aunty ta shigo ta riko hannun mamanta gam, kallonta take tana hawaye tana tuna irin tarin cutar da ta yiwa iyayenta da kanwarta dan son kanta, kamar yanda bokanta ya fada in dai suka ji sunnan Mama toh zasu tuno da ita ne da muguwar soyayarta a ruhinsu hakan ya sa ta kafe mahaifiyarsu da ido ta ce" ummey, ina MARIAMA take Tamkar bugawar guduma haka sunnan ya shiga kwakwaluwar Ummiey daya bayan daya, wanda a nan ta zube sumamiya............ 💓 *❣IDAN KA RAINA INDA KAKE❣* Na: *SAJIDA* *_LITATAFAN MARUBUCIYAR_* *_Duk Karyar kada_* *_Yar Mahaukaciya_* *_Neman na kaina_* *_Bani da zabi_* *_Daga tafiya daukar soja_* *_Idan ka raina inda make_* *🌈KAINUWA WRITERS✍🏼 ASSOCIATION*🤝🏻 ```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}``` https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation 6⃣4⃣ *Nd* *ND* *ND* ALHAMDULILAH *DUBUN GAISUWA DA FATAN ALKHAIRI GA YAN GUDAN MU, KAINUWA WRITERS ASSOCIATION, FATANA ALLAH YA KARA DANKON ZUMUNCI YA KARE MU YA SHIRYAR DA MU YA KARA HADA KAN MU YA KORE FITINA YA BAMU LAFIYA YA KARA MANA ARZIKI MAI ANFANI, TAKU CE KANWARKU CE YARKU , YAYARKU CE, KAWAR KU CE YAR MUTAN NIGER* Rikicewa Aunty ta yi tana faman ihun a taimaketa, nan mai aikin gidan ta zo ta kamata domin qbin ya ja baya sosai ba masu aiki da yawa wannan din ma tana tare da su ne dan amana, Kamata ta yi suka yi daki da ita inda Sarah ta samu waje ta zauna sai susa take hannunta cikin sket dinta kowa na kallon ta Kamar wasa har yama ta yi ummiey bata farka ba har lokacin da dady ya dawo daga aiki Yana zuwa ya tarar da tashin hankalin nan, Nan ya shiga tambayar ba.asi aman da yake ta ga yanda ummiey ta yi sai tsoron fadawa dady ya kamata, Kanta kawai ta sada tana sharar hawaye inda shi kuwa yace su kamata a je asibiti mana tunda bata farfado ba, Tashin hankalin da ya tardo ummiey a ciki ne ya hana shi gane hallin da su Aunty ke ciki dan haka suka kamata suka nufi asibiti Likitoci ma sun rufu a kanta su dai basu ga abinda ya sumar da ita ba, kuma sun yi mata yanda ya dace ace ta farfado aman shiru kake ji malan ya ci shirwa Lokacin da docter yake fada masu aunty ta dora hannayenta a kai ta rushe ta kuka ta ce" shikenan na cuci kaina, ni ba ga gidan mijin ba, ni ba ga konciyar hankali ba, gashi zan rasa mahaifiyar tawa , wayo mariama ki yafe min abinda ba yi maki a rayuwa na raba ki da iyayen mu dan tsananin kishin irin yanda suka damu da rashin lafiarki gashi tana neman kome mani tun a gidan duniya ina haduwa da abubuwan da suka girmami tunanina, bokan kansa ya mutu wanda na dogara da shi na manta Allahna Tunda ta ambaci mariama Dady ya zaro ido ya maimaita sunnan a lebensa, kafin ya gama fada ya yanke jiki shima ya fadi nan wajen sumame, wanda sai daga baya wata nurse ta kwala ihun wani ya fadi Nan mutane sukai kansa shima ana kuma kallon aunty dake ta dumumuwa tana fadin" shima dadyn ya tafi ko? To ai shikennan ni zaku yiwa haka ko? Du ku mace ku barni da duniyar ko? Nima sai na mutu, nima mutuwar zan yi ehe Aunty dai an fara sakin layi domin magangannunta na wanda baya cikin hayacinsa ne Docten nan shi ya rufe daman likitan dady ne ya nemi wani baban malami shek ne ya fayace masa abubuwan dake faruwa Shek din ya nemi da a zo da su dan haka doctern ya samu da kyar aunty ta sa hannun yarjewarta a fita da su ya shiga ya fita ya samu ambulence din asibitin aka saka su ciki aka fita da su sai gidan shek ibrahim Ana zuwa ya tara almajirai aka shiga karatu, yi suke ba gajiyawa har zuwa wani lokaci ummiey ta fara wani irin abu kafin take amayo wani bakin abu can kuma sai ta shiga sauke ajiyar zuciya...... Dadynma kusan hakan yayi sai dai shi kan yayi aman sai da aka jima sosai har sai da ummiey ta kawo hankali tana kuka tana fadin ina Mariama? Mariamarta, Gaba daya wajen ba wanda bai tsorata da duniya da abinda ke cikinta ba a lokacin da aunty ke tonawa kanta asiri ba tare da an matse bakinta ko an tilastata ba(sanu sanu bata hana zuwa, hakuri maganin komai) , Ummiey ta girgiza ta yi kuka har ta gode Allah, tana yiwa Aunty kallon tsoro ta ce" ina kika kai min ita bayan kin rabani da ita? Ko kasheta kika yi? Cikin kuka aunty ta ce" ya zan kashe yar uwata ummiey? Ummiey ta ce" kul da bakinki , kar ki kara wani abin na munafurci, mai halinki idan ba Allah ya kama shi ba, yayi masa muguwar kamu baya daina aikata mugun abu a doron kasa....... Aunty ta sada kanta, ta ce" tana nan a anguwar yawa, tana tare da mijinta malan ahmad da yayanta biyu, karamar an yi mata aure tana auren Elhaj Sudais Uban masu gida A tare ake furta ikon Allah, masha Allah, Ummiey kam mikewa ta yi ta tayar da balin kawai su je su tafi su je Hakan kuwa aka yi shek ya tayar da mota biyu dayar warda ake masa jigila ne sai wace yake hawa suka shiga Aunty na fadin wajen har suka karasa kofar gidan Malan na da sai dai kamar Aisha katon shago suka tarar da ma.aikata, aman wannan karron malan a kofama yake suna zaune suna kukula goron sadakin Humaira da ya karba a ranar an kawo sadakin naira dubu hamsin da huhun goro biyu suna kulawa ne dan jama.arsu Tunda Aunty ta fito gabansa ya fadi, Allah yana ganni baya son huldar yan uwan biyu shi ya sa yaki nuna kansa karma ta ga inda suka koma Sai dai me, idannuwansa suka sauka kansu, duda an manyanta ba zai mace iyayen matarsa Hajiya ummiey, mace har mace mai isa da takama mai juya ragamar gidanta mai mulki ta tsofe sai dai duda haka da ciwo da tsufa daban take, wannan baiwa ce daga Indallah Da sauri ya taso ya nufo su, wanda suma suke binsa da kallon mamaki da kuma kunyarsa Iso kawai yake masu kan su shiga gida su je Suma ta ciki ya ratsa da su har boyayiyar kofar gidan nasu, Da mamaki du suke kallon tsarin gidan, motama biyu ce tankama tankama, gidan ya linka na aunty hakama ya fi na su ummiey nesa ba kusa ba, maganar tsaruwa kuwa ya ginu ginnin zamani duda sun ki a baza tils sai farar kasa solsolsol dake share tana mugun daukan ido da dadin takawa A wannan rana an sha kukan farin ciki, mama ta rasa ina zata tsoma ranta, inda ana haka Aunty ta zame ta tsere, kunya ta hanata zama , zuciyarta ta kasa gaskata mata Mariama ce haka, lale duniya sai Allah , ka ga du ya barsu sun gama hayaniyarsu ya sakawa abin tsari , hakan ya kara karyar mata da zuciya ta sabi hanya a kafa dan komawa gidan ta san abin yi tana matukar jin kunyar iyayenta da wuya ta iya ci gaba da zama tare da su Mariama ta yi kukan halin da Aunty ta shiga da yarta domin a gidan malan sai da ta fayace masu komai da komai, harma ta ji tana son taimaka mata (🙄), Bayan kwana biyu Yau suke dawowa daga tafiya, , a cikin jirgi a jikinsa kawai take hannunsa a saman mararta ta cikin hijabinta A hankali ya rada mata" Alllah ya sa ki sama min yan hudu Mata, na kagu su fara motsi , na kagu ya kara girma na ganki kina tafiya irin na masu ciki, Mata idan kika haihu zan ta daukan babyna ina kallo, Allah ya nuna min Bata ce amin a fili ba dan matsananciyar kunyar abin take, wai ira rauda daga aure sai ciki, gara ta dawo daga tafiyar da ba salama sannan ta shigan masu da ciki Ita dai ta godewa Allah, shi kuwa baya jin kunyar hakan yayi ta lagudata kennan yana santin cikin Ki yi magana mana, na fasa kai ki gannin maman da mun saukan! Ya fada yana hade fuska irin da gaske yake Ai da sauri ta ce" amen *MIJI* yayi murmushi Mota na tsayawa kofar gidan da yace wai su mama na ciki, nan ne gidansu ta bude marfin motar da gudu gudunta zata arce Wata sufa yayi ya fito a mitar da Samir ya dauko su ya kwala ihun" MATA idan kika yarda kikai gudun nan da cikina sai kin haihu ke da gidan nan An yi katari Aba ya fito da leda daga cikin gidan, komai a kan kunnansa, Samir kansa da ya saki baki idannuwansa suka sauka a kan Aba ya kara buda bakinsa ya dora hannayensa a kai Bai gama tantance komai ba Ya ji Sudais na fadin" idan baka tayar da motar nan mun bar wajen nan ba sai na shake ka Samir Samir ya zabura ya waigo ya ce" oga ai Aba ne baka gaishe shi ba Sudais ya ce" SAMIR😤 da sauri samir ya tayar da motar yana dariya a fili ya dan fitar da kansa yana gaishe da Aba a take kuma yana faman yin kwana da motar ABA kam dariya abin ya bashi sosai irin yanda Sudais ya sada kai ba zai iya kallon Aba ba bayan wannan baranbaramar da ya yi................. Daga nan ya umarci Samir da su je gidan su Humaira Sun kusa karasawa Samir ya kara kallo sudais akai katari suka hada ido wanda an yi haka ya fi a kirga,, Sudais ya ce" ka kuma kallona Samir zan saukeka ne a motar nan Samir ya zaro ido ya ce" oga motana ne fa Sudais ya ce" to ka sake ka gani Samir ya yi murmushi ya ce" daman murna nake, kuma ina fatan Allah ya raba lafiya Sudais ya ringa sakin kasaitacen murmushi yana shafa sajensa a zuciyarsa yana amsawa da amin, Can bayan sun tsaya cikin gidan su Humaira Sudais ya ce" ka gane ko, ai ita *MATA* yanda ta so kawai hakan ake yi, kai Allah ja da zamanin *Mai Ni* Dariya kawai Samir ya bushe da ita gannin da gaske Sudais din ne ke haka, lale duniya Da iyayenta ya gana inda ta labe tana kallonsa ta bayan labule Sosai sukai godiya tare da fadin yanzu za.a rakata, Allah ya kara shiryar da ita Cike da jin kunyarsu ya baro gidan, Yana tafiya Mom da kanta ta saka ta yi wanka suka sakata gaba suka kara yi mata nasiha da fada da alkawarin idan haka ya jara dawo da ita ta san abinda zata tarar Har kasa ta duka tana mai neman gafarar su kafin suke tafiya mama ta kaita har gidanta ta dawo (Wannan kennan, ) Tunda ta shigo take faman sai sun yi hira da Aisha aman ta lura sai sada kai take , kunyarta take ji kamar ta mutu.....wai a haka ta je har gidan kanwarta gaban mijinta tana zuba hauka? Wohohi ai ita bata fatan abinda zai saka ta ganta gata ga sudais ba, ba zata iya kallonsa ba dan tsananin jin kunya Rauda kuwa sai murnar har an fitar da anko din biki take ta kasa zama sai murna take ta je ta zaga shagon Abanta, sam bata san irin abinda mijinta ya yiwa iyayenta kennan ba, wannan lamari ya saka ta kara zage damtsen sai ranar da numfashinta ya bar gangar jikinta zata daina kokarin faranta masa........ Bayan wata tara Shayar da Umar Faruk take tana kallon yanda Sudais ke sakawa NANA FATUMA pampos Dariya ce ta kwace mata gannin a baibai ya saka mata, Humaira ce ta yi salama ta shigo da fida a hannunta ta dafo shi, ta ce" oh my god malan karka jirde min kafar ya mana Tana fada ne tana kokarin karbe Fatuma a hannunsa Zama ya yi yana sauke ajiyar zuciya, watan yaran biyu domin a wata takwas ta haife su aman masha Allah jibga jibga da su, nononta mai kyau ne.........., kallon yanda Humaira ke sakawa yake, da dan cikinta na wata biyu abinka da marar jiki har ya fara dan shaida kansa Rauda ce ta dan rike kujerar da take sama ta rintse idonta, cikinta ke ti mata ciwo kwana biyun nan bata san dalili bA Humaira ce ta ce" cikin ne Rauda? Rauda ta lumshe idannuwanta, bata son tace cikin ne ya hana tafiyar domin shiryawa ne suke zasu je fitar da ankon auren Samir da Hafsat Sudais ya mike ya fita da wayarsa Ba.a jima ba suka dawo da docter Amina, nan ta tsareta da tambayoyi dan gane ko wani abin ta ci? Sai dai amsar bata gamsar da ita ba dan haka ta saka ta shiga ta bata fitsarinta Tana dariya tace" kai docter gashi, ni dai dan aikinki ne da sai nace me kuma za.a yi da fitsarina Murmushi ta yi itama ta bude abin awon ciki irin na pharmaci mai tsadar nan ta saka kan cikin fitsarin Raudar Kamar da wasa ya nuna tire biyu Rauda tace aa a sake ai yana bada ba hakaba Sudais ne da kansa ke barewa yana sakawa cike da zumudi, Rauda kuwa hawaye har ya fara wanke fuskarta, Result din dai daya ne, ciki ne da ita wanda daman wancen ma haka yayi ta sakata ciwon mara kafin yake zama da kyau, sai dai basu san ko na sati nawa ba Kuka ne ta fashe da shi hannayenta saman kanta, Humaira kuwa sai juyi take tana fadin wayo.gidanmu zai cika da babys Gannin da gaske kuka take ya saka Sudais ya kama hannunta ya nufi dakinta da ita Suna shiga ya zauna bakin bed ya dorata saman cinyarsa A hankali ya ce" menene? Rauda ta dago ta sauke idannuwanta cikin nasa, murya a raunane ta ce" Aban Yara, yaushema na haihun? Abansu na sha wahala sosai, kar kuma a zo ana fadin bani da aiki sai haihuwa Murmushi yayi ya ce" zabi ya rage naki *Mata*, ki kontar da hankalinki, ki rainar min cikina, ki kara haihuwa , ki bani farin ciki sannan gobe kiyama mazon Allah yayi alfahari da mu domin yace mal.umarsa ta haiyayafa domin gobe kiyama yayi alfari da mu..... Ban ki ba aban yara, Katseta yayi ta hanyar dora yatsarsa kan lebenta ya furta" shiiiiit, bana son ki bata min rai a irin wannan lokacin, bana son na ji haushinki dan kin ki taya ni farin ciki.......wannan dai cikina ne, ni na yi abina, ina son abina Mata ina son ki, ina son kon ki, ina son kasancewa da ke.....tsoronki shirmenku na mata ne kar ki tsofe......mata koda ciki ya mayar da ke wata kala ina son ki a haka......ki daina Da murmushi ta rungume shi, a hankali ta ce" ka san ba kishi nake ba...juste ina tsoron a kuma shigar min gonata ne dan kasawata ta wani fannin, koda zaka kara bana so dan na kasa sai dan ra.ayinka Murmushi yayi kawai, ya mayar da ita kasansa ya haye bed din tana ji tana gani aka shiga kwallon....tafiyar da sai .....m..mm.... *Alhamdulilah* An gada a nvl, kai a komai ma ya kasance ka batawa wani, wani bai so ba......ku yafe min, Allah ya bani ladan dake cikin nan ya kuma yafe min kurakuran da na tafka...... Daga *YAR MUTAN NIGER, SAJIDA MAMAN LALLA* Mu hade a *BAK'A CE......IN SHA ALLAH* Complete by ummu hafeez the writer of 'yan matan amarya and Komai mukaddarine Bye bye