[19/07, 7:44 PM] Halimatu A/rahman Sadeeya: 📝🍇✨💫⏰🤴🏻👹❤️❤️❤️ بسم لله الر حمن الر حيم... 2:03 Pm. Friday 4 February 2022. *SAKAYYAH* *GARKUWA SABON SALO* Book One, page 1 NA *AYSHA ALIYU GARKUWA* 🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 *FREE PAGE* *Komai na rayuwa sai Allah ya nufa, kugafa Time and Date din da na fara rubata littafin nan amman sai Allah ya bani ikon fara sakinshi.* Wannan littafin nawa mai suna FATTANAH kirkirerren labarine, Amman akwai wasu abubuwan dama da sun faru da gasken gaske, banyi da wata ko waniba, Hakkin mallakarsa nawane AYSHA ALIYU GARKUWA, ban aminceba! ban lamunceba!! ban yardaba!!! ayimin amfani da labarin littafina tako wacce sigaba, har sai in an nemi izinina an samu sahalewata, sabida haka ga number ta 09097853276 kafin ayi komai a nemi sahalewata, komai yafi daɗi cikin mutuntaka zama lfy yafi zama ɗan Sarki!!!.. *Yah Allah ka bani ikon rubuta al'khairai da abinda zai amfani al'ummar fiyeyyen halinta, Ya Allah kayi riƙo da hannayena, tunanina, idona, yatsuna, nazarina, ka hanani samun damar rubuta duk wani abin ƙi da zai zamewa al'ummar musulman masifa ko ƙazanta ko bata tarbiyya, ya Allah ka bani ikon tunasarwa da jan kunne da jan hankali ih zuwa ga nasarar mai tawakkali da imani da riƙo da ibada, Ya Allah ka nuna min ƙarshen littafin nan lfy kamar yadda ka nuna min forkonsa Lfy dani da iyayena ƴaƴana, yayuna, ƙannena, da maƙota makaranta na masu biyana kafin su karanta da masu karanta na sata da dukkan musulmai ya Allah ka nuna mana forkonsa da ƙarshensa lfy kayiwa rayuwarmu data ƴaƴan mu al'barka ka shirya mana ahlinmu ka bawa yayanmu mata maza na gari, mazan ka basu mata na gari, aurarru ka basu zaman lfy da zuri'a ta gari ka tsare mana tarbiyar yaranmu bisa tafarkin dai-dai. Ya Allah kayi mana rufin asiri duniya da ƙiyama, ya rabbil izzati ka dubi bayinka masu buƙatan haihuwa da aure da idanunka masu rahama ka basu masu albarka, marasa lfy Allah ka basu lfy masu juna biyu Rabbi ka sauƙesu lfy masu fama da matsar babu da bashi ya Allah ka yalwata masu ka basu arziƙi mai albarka la basu ikon biyan bashi, Ya Allah ƴaƴan musulmai da tatbiyarsu ke a gurɓace Allah ka shiryesu. Ya Allah ka kawo mana sauƙin wannan zadar rayuwar, ka magance mana fitintinun dake damun ƙasarmu, mahajjatsnmu kasa sunyi hajji Mabruk. al'farmar Annabi da al'ƙur'ani, ya Ubangijin talikai ka jiƙanmu ka yafe mana kurarenmu kayi mana Kekkyawar ƙarshe kasa mucika da kalmar shahada yayin barinmu duniya ka sadamu da mala'ikun rahama masu zaran rai salamun salaman. Yah hayyu ya ƙayyum birahamatika astaƙisu ka jiƙan mahaifiyata Fatima (Deddena) ka sanyaya mata makwanci ta ka haskaka mata ƙabarinta ka yelwata matashi ya Allah kasa tana cikin dausayin jannatul firdausi ya ubangijin kasa can yafi mata nan, ya Allah ka bamu haƙurin da juriyan rashinta. Ya Allah kai mata rahama al'farmar Annabi da al'ƙur'ani🙏🏻😭😭😭* ~Aisha Alto, Mom Bobo, kune wanɗa nake ganin kamar kunsan ciwon da nakeji a raina a duk sanda na tuna banda mahaifiya, domin kusan lokaci daya muka rasa iyayenmu. Allah yayi musu rahama yasa sun huta, ina tunawa a lokacin nafi son yin mgn daku fiye da kowa a social media, domin gani nake kun san yadda nakeji a zuciyata, Aisha Alto addu'o'in da kikeyi min dani da mahaifiyata yasa nakejin ke ta dabance mom bobo kuwa munsha kokawa tare, mu rasa mai lallashi wani tsakaninmu~ *Littafin SAKAYYAH na kuɗine 1k ne kacal wannan Free page, yar uwata ki biya ki karanta abinki cikin Salamah 0661110170 GTBank AISHA ALIYU GARKUWA, sai ki turo min shaidar biyanki ta WHATSAPP 09097853276. In baki da account zaki iya bada a P.O.S ki Basu 100 na su turo 900 wasuma 50 suke amsa, ko kuma ki sayi katin Mtn sai ki copy number's ɗin katin ki turo min ta WHATSAPP. Banda V.T.U. dan Allah.* A hankali ta turo ƙofar ɗakin nata, cike da jin nitsuwa da salamar, sanin ta yanke baccinta ne ta tashi cikin talatainin daren, domin neman aminci da yardar ubangijinta daya halincceta ya bata rai da lfy, cikin rashin tsoron da ko yaushe in ta tashi tsakiyar dare, Allah ke yaye matashi, duk da kasancewar makaken gidane bila haddin wanda ke kewaye da tsirrai, kana ga wutsiyar kogin Gembulan na jihar Taraba da yayiwa gidan zanen harafi C, yayinda kuwa su biyu ne rak suke rayuwa a cikin ƙaton gidan. Koda yake tazarar dake tsakanin ɗakinta da sade ɗin jikanta Modibbo tazarace mai yawan gaske, sai dai suna raya gidan da Ambaton Allah a koda yaushe, shiyasa ubangiji yake saukar musu da cikekkiyar nitsuwa salama. Numfashin ta fesar a hankali tare da gyara ɗaurin zaninta, kana ta gyara riƙon da tayiwa yar butar dake hannunta. Ido ta lumshe tare da buɗe su a hankali, sabida wani irin sassayan iska mai masifar daɗi da ratsa jiki da taji yana ratsata da sakar mata wani irin nitsuwa, salama, da farin ciki. Juyowa tayi ta kalli yamma sabida ganin wata ta faɗi alamun dare ya tsala, domin watan tayi kwana goma sha ɗaya ne, faɗawanta ke nuni da biyun dare ko ɗaya da rabine. Kai ta ɗan juyo gabas ta kalli ƙofar safe ɗin Moddibo wanda yake can nesa da ita sosai, yayinda wasu sassayan fulawowi yayiwa ko ina na gidan ƙawanya. Tsarin ginin gidan tsarine, wanda ko a ƙasashen turawa na musamman ne, Ƙaton gidane mai yalwar fili. Daga can bakin gate ɗin gidan filine mai girma wanda zai iya ɗaukar motoci shida ba tare da wata ta gogi wata ba, ko matsi wataba, ɗakine mai ɗan girma a bakin gate ɗin wanda ke haɗe da bayi a ciki, da yar baranda alamun ɗakin mai gadi, saidai babu kowa a ciki. Daga gefe kuwa watsu tsala-tsalan bishiyoyin na mijin gwanɗa ne masu masifar tsawo da ganye mai duhu a can sama sune suke jere reras a jikin katangar gidan baki ɗaya, daga ƙasansu kuma, wasu tsirran fulawowi ne masu masifar kyau da sanyi masu collor's blue, red, and yellow. Tsakanin farfajiyar gidan da can cikin gidan kuma, akwai wani katanga a tsakiyar da kuma ɗan madaidacin gate shima ɗin mota zai iya wucewa ta nan, Cikin katangar shima zagaye yake da bishiyoyin dabino ta wajen ta cikin kuma in bishiyoyin mangoro ne guda biyu sai daya gefen kuma na goiba, ne da kuma cabɓulle (Tsada) akwai fili ta gefen hagu, inda motoci biyu zasu iya tsayawa a wurin. Sai gefen dama kuma, wani ɗan siririn hanya ne, wanda fulawowi ne yazama kamar katangar wurin, tafiya kaɗan zakayi ka riski part din Moddibo, irin ginin nanne mai tudu, duk da bawai bene bane amman ginin a sama sosai yake, forko daga wurin baranɗace mai girma, da tudu wacce ke malale da tayis mai masifar sheƙi, a bakin barandar anyi wasu steps guda bakwai masu faɗi, kafin hawa barandar, A gefen dama da hagunsa kuwa wasu fararen ƙarafun silver ne masu kyau sukayiwa barandar garkuwa, a ƙasansu kuwa, wasu. Tukwanen ƙasane masu tsirran fulawowi masu masifar kyau da ƙamshi, kana a kan ko wanne step akwai tukanen a gefen hagu da daman a jere, guda bakwai-bakwai kenan. In ka gama haurawa saman barandar kuwa ka juyo ka kalli bayanka ras zaka hango tekun Gembilan kwance a can, da tsirran bakin Kogin. A can bayan Part ɗin nashi kuwa wani tamfatsetsen garding ne mai masifar kyau da ƙamshi, sai wani tabkin wanka mai kyau kujeru guda bibbiyu a kusurwowin alƙibila, sai kuma gado a gefen dama da hagunsa, Cikin Part ɗin nasa kuwa, wani tamfatsetsen parlour ne mai kyan tsarin ƙasaitattun kujeru da labulaye da kayan wuta, komai na ciki farine tas, tambarin shaidar tsananin tsabtar ma-mallakin wurin kenan, sai ɗan ratsin sky blue, wanda hakan yasa in ka shiga falo sai kayi zaton a sararin samaniya kake shawagi. Sai dinning area, da kuma kitchen, sai wani yalwataccen corridor'n wanda ke gefen dama da hagu ko wanne bedroom ɗaya ne a ciki, sai can mashigar falon nanma akwai wani ɗan madaidaicin bedroom. Hatta cikin falon kuwa kewaye yake da fulawowi, shaidar ma-mallakin wurin masoyin sirraine da sanyi da kamshi window palon irin manyan nanne har kusan ƙasa, haka yasa yana iya hango bakin tekun daga cikin palonshi. Daga Part ɗin nashi kuwa gefen hagu akwai wata hanyar mai kewaye da tsirrai, wacce ke sadashi da can cikin gidan. inda ɗaki ɗaya ne rak, na kakarsa Innayi wacce tace ya isheta rayuwar duniya. Sai kuma kitchen nata a gefe mai tsarin gargajiya, kana da bayan gidanta can gefe, domin sam taƙi yarda ayi mata bathroom a cikin ɗaki, acewarta kada santsin tayis ya ƙaryata, dole haka Modibbo ya haƙura da tsarinta komai na gargajiya, hatta gadonta taƙi a sauya mata. Sai dai ta amince da tsarinsa na zageyesu da tsirran shuke-shukensa da zuba mata tattausan Turkey carpet mai masifar taushi, tsarin dakin nata komai ya fito kamar na gidan sarakai shuke-shiku kuwa ba dama. Daga can gefen hagun side nashi, wani wurine mai ɗan tudu wanda akayiwa rumfa irin ta gargajiya rumfar bunu, gefenta zagaye, da tsirran, cikinta kuwa wasu tsala-tsalan kujerune masu masifar kyau guda hudu da table a tsakiyar su, sai ɗan dandamali na al'adar mutanen Gembilan wanda suke hura wuta a ciki sabida rage tsananin sanyin da ake tsula musu. ALLAH kuma ya yelwata hannunsa da al'barka duk abinda ya shuka sai ya tsiro a yalwace. (Moddibo kenan) Numfashi Innayin ta sauƙe lokacin da ta gama ƙarewa farfajiyar gidan da lukkunan gidan kallo, duk da ba hasken farin wata, babu kuma na taurari sosai, sakamakon hadarin gajumaren da yayiwa sararin samaniya ƙawanya. Juyawa tayi ta nufi, ɗan bayan gidanta dake, nan gefenta kaɗan, tana maiyin taku cikin yanayin tsufar da ya cinmata, tare kuma da taka tsantsan gudun kada santsin simintin dake malale a farfajiyar sashin nata ya kadata. A bakin ƙofar bayin ta ɗan tsaya tare da yin, addu'a shiga bayin. “Allahumma inni'aauzubika minal kuɓsi wal kaba ihsi”. Kamar yadda Moddibo ke nusar da ita mahimmancin addu'a ako wanne lokacin. Bayan ta fito ne, da addu'a a bakinta, ta zauna bisa, wani dutse mai kyau dake bakin barandar ɗakinta, ta fuskanci gabas. Tare da fara al'wala. A can side ɗin Moddibo kuwa, kwance yake, harshensa jiƙe da ambaton Allah, duk da cikin bacci yake. Saidai baccin, ba baccine kamar na kowa ba, domin bacci yake cikin wani irin yanayin daya gaza tantancewa, shi ba bacci ba, kuma ba ido biyu ba, ba kuma mafarkiba ba kuma zahiri ba, ba kuma a sumeba wasu abubuwan da lokuta da dama yana riskarsu cikin bancinsa yake fuskantar su. Ita kuwa Innayi a hankali ta gyara zamanta, tare da juyowa ta kalli bayanta, da sauri sabida wani irin haske da taga ya gilmawa ganinta, sai kuma tayi saurin juyowa gabanta ta, kalli gabas saitin ɗakin Moddibo domin a zatonta ko an dawo da wutar nepa ne. Ga mamakinta kuwa, babu alamun hasken wutan nefan sai wani irin sanyi mai ratsa jiki. Haka nan taji wani yanayi na rufeta, wanda yafi kama da tsoro abinda bata taɓa fuskarta sa acikin gidanba duk duhun dare. Hakan yasa tayi saurin sunkuyar da kanta taci, gaba da yin al'wa'ar, hannunta ta wonken, kana ta ciko tafin hannunta na dama da ruwa, zata kai bakinta domin kuskuran baki kenan. Wani irin saurin ɗago kanta tayi ta kalli gabanta, sabida ganin wani irin masifeffen haske mai firgitarwa da taga ya haska illahirin duniyar har hasken yana haska cikin ruwan dake tafin hannunta. Cike da tsoro ta zubda ruwan tare, da juyawa ta kalli. Gabas da yamma Kudu da Arewa. Babu mutun ba dalilinsa, babu kuma alamun ta inda hasken ke fitowa. Kana kuma ga kuma hasken dake tsananta. Da wata sassayan iska mai ratsa jiki da sanyaya zuciya. Wacce tasa Moddibo gyara kwanciyarsa tare da ci gaba da wani irin bacci mai mayataccen daɗi da yaji ya dannesa da kuma shigo masa da wasu sabbin ababen gani a idanniyansa, yayinda harshensa kuwa ke nanata addu'o'in masu tarin yawa. Yayinda ita kuwa Innayi, wani irin tsuma jikinta ya farayi lokacin da taga gaba ɗaya duniyar ta ɗauki wani irin mashahurin haske mai kyan gani. Wanda ta rasa ta ina yake fitowa. “Innalillahi wa innailaihi raji'un hasbunallahiwani'imanwakil”. Ta fara maimaita cikin firgici lokacin da ta ɗago kanta, ta kalli sararin samaniya. Wani irin kerma da makerketa mai cike da tsananin tashin hankali, firgici, tsoro, da karkarwa jikinta ya farayi, sabida yadda taga ubangijin talikai, yana wanzar da ikonsa da buwayarsa a sararin samaniya. Wasu irin masifaffun hawaye masu zafi wanda irinsu kan tsinkowa ɗan Adam lokacin da yaga tsananin abin tsoro da shiga firgici da ƙudurar Allah. Kar-kar haka jikinta yake rawa, ganin yadda taurari. Suke fizgowa sunayin wani irin haske mai kashe idanun ɗan adam, wanda sune take ganin duk sun cika sararin samaniya da haske tamkar rana. “Ya hayyu ya ƙayyum birahamatika astaƙisu, ya Salam, innalillahi wa innailaihi raji'un, la haulawa ƙuwta illabillahil aliyul azeem”. Sune tasbihai da furucan da ubangijin ya bata ikon furtawa, lokacin da ta fara ganin taurarin sunayin ƙasa tamkar zasu faɗo, ƙasa domin gani take kamar sai sunzo har ƙasa sosai kamar zasu taɓo rufin kwanon ɗakin Modibbo, sai kuma taga ubangijin ya janyesu sun koma sama da azaban sauri tare da tartsatsin haske mai kyan gani. Fadin halin tsoro ko tashin hankali ko firgici da ɗimuwar da take ciki ya zarta zaton mai zato, ya wuce tunanin mai tunani ya shallake nazarin mai nazari, wasu irin wahaye ne ke kwaranyo mata. Yayinda ta koma baya ta jingina bayanta da jikin filan barandar ɗakinta dake bayanta, ta jingina kanta tana kallon sama. Tare da fara nanata kalmar shahada. Domin ta gama sallamarwa cewa, lokacin ta yayi, ma'ana mutuwa zatayi. “La hailahaillahu Muhammadu Rasulullahi sallahu alaihi Wasallama”. Shi ta fara maimaitawa can ƙasan maƙoshinta domin. Komai na jikinta ya fara tsayawa, sabida azabebben tsoron daya rufeta da cikekken imanin kaɗaita rabbissamawati wal ardi zuwa yanzu tama fara ɗimautan shin anyama kuwa a raye take?. A ƙalla 30 minute ubangijin talikai na wanzar da ikonsa! Da kuma, buwayarsa!! Can kuma sai ta fara ganin gaba ɗaya duhu na meye hasken. Duhu mai cike da sassayan iska. Wani irin tsorone ya kuma rufeta wanda ya diro mata da zazzafan zazzaɓi mai haɗe da masifeffen ciwon kai. Wanda ya tilasta mata kife kanta bisa guiwowinta tare da rumtse idanunta tamkar zata liƙesu da juna. A can cikin masarautar Gembilan kuwa, Gimbiya Dadu ce, ke kwance bisa tsakiyar gadon ta, wani irin masifeffen mafarki mai tada hankali takeyi. Wanda yasata ihun neman ceto, wanda bata saninba har ya fito fili. Fitarsan ne, yasa hadimarta saurin shigowa tare, da tadata. Ai kuwa cikin tsananin firgici da tsoro ta farka tana mai karkarwa, lokaci guda kuma zazzafan zazzaɓi ya rufeta. A nan gidansu Moddibo kuwa. A hankali ya fara buɗe idanunsa tare da ambaton Allah. Hannunsa yasa bisa bed side drawer ya jawo wayarsa. Gefen wayar ya ɗan taɓa da yatsarsa manuniya, wanda hakan yasata kawo haske har ya haska Kekkyawar fuskarsa mai cike da yalwataccen saje mai sulɓi da ɗan madaidaicin gemun da bazai uwace kamu ɗaya ba yayiwa siraran jajjayen leɓɓansa masu sheƙi ƙawanya. A hankali ya ziro ƙafafunsa ƙasa, sabida ganin, ƙarfe huɗu saura kwata. Bathroom ɗinsa ya nufa. Yana shiga yayi brush da wonka tare da yin al'wala, kana ya fito. Durowarsa ya buɗe yayinda yake amfani da wayar hannunsa wurin haska abin nemansa domin har yanzu babu wuta kasan cewar yanayin garin Gembilan garin mai masifar sanyi mai daɗi, yasa basu cika damuwa da rashin wutar da ƙasartamu ke fama dashi ba. Wata tattausar jallabiya fara ya zira kan ƙananan kayan dake cikinsa, tare da jawo farin hula taɓa kaji hadis a kansa, turaren Oud bakhur mai masifar ƙamshi ya fesa, tare da sa hannunsa na dama, ya zaro carbinsa kana ya fito, falonsa, tare da sassarfa ya buɗe ƙofar falon ya fito. Can cikin gidan ya nufa kamar kullum domin tabbatar da cewa kakartasa ta tashi daga bacci duda yasan kullum bisa sallaya zai sameta to amman hakan baya hanasa zuwa. Ɗan tsayawa yayi tare da kallon inda Innayi ke zaune har yanzu, yadda kanta ke kife bisa guiwarta sai yayi kamar tana sunkuyene irin zata wonke fuskartan nan. Da ɗan sauri ya juya ya nufi bakin gate nasu yana mai tasbihi. Ƙarami ƙofar dake manne jikin gate ɗin ya tura ya fita asalin farfajiyar babban gate din nasu, A hankali yake motsa laɓɓan bakinsa, yana taibihai, tare da shaƙar sassayar iskar, A hankali ya kuma buɗe ƙaramar kafar kana ya nufi masallacin jumma'a dake layin nasu wanda yana kallo tamfatsetsen gate din gidan tsohon gidan Alhaji Abubakar Mafindi mahaifi ga Amininsa M Jamil kenan. Ita kuwa Innayi ƙamshin turarensa ne, da kuma motsinsa ya tabbatar mata shine, so take ta ɗago kanta amman ta gaza, sabida wani irin sarawa da kanta yakeyi. Har yanzu sunan Allah take kira, a ƙalla mintuna 20 da fitarsan kafin Allah ya bata ikon motsawa, Cikin ƙarfin hali ta ɗago kan nata, lokacin da taji sautin murya Jamil yana kiran assalatu. Wasu irin zafafan hawaye ne suka tsilalo mata wanda tsananin ciwon kan ne ya jaza mata su, Cikin ƙarfin hali tayi, al'wala tare da yunƙurawa ta mike tsaye tana mai dafe kanta, ta koma, cikin ɗakinta, dai-dai lokacin kuma aka dawo da wuta, yayinda ko ina ya gauraye da haske, sallaya ta shimfiɗa kana ta zira hijabinta, ta fara nafila, jiki na rawan zazzaɓi da kyarman tsoro tanayi tana mamakin shin wai ashe a raye take?... Ƙarfe bakwai dai-dai na safe. Ya shigo gidan, maida ƙofar yayi ya rufe, tare da ɗan tsayawa, tsakiyar gidan, yana mai kallon ƙofar kitchen ɗin, Innayi yana mai nufar cikin gidan. Agogon hannunsa ya kalla, tare da ɗan jinjina kai sai kuma ya juya, ya nufi, side ɗinsa, yana shiga bathroom ya wuce, ƙofar ya maida, ya rufe, tare dasa hannunsa ya jawo, tattausan towel, ya ɗaurasa a ƙugunsa bayan ya zare, jallabiyar, da vest, yana ɗauke da towel, sassayan numfashin ya fesar kana ya shiga cikin jaccuzie ɗin. Cikin nitsuwa yayi wonka fes, ya fito. Yana wani irin masifeffen ƙamshi yayinda gargasan jikinsa ya kwanta lib a tattausar farar fatarsa da damshin ruwa, Wani towel ɗin ya jawo ya ɗaura, kana ya zare na ƙasan, matseshi yayi tare da shanyasa. Sannan ya fito yana mai tsane tattausan sumar kansa da ƙaramin towel ɗin. Gaban dreesin meeror'nsa ya tsaya, ya fara kimtsawa, cikin yanayin nitsuwarsa da rashin yin abu da gaggawa... Bayan ya gamane ya fito fes yana baza ƙamshi mai masifar daɗin shaƙa, sai wani irin kyalli sajensa keyi, yayinda jajayen lips ɗinsa suke wani irin sheƙi tamkar dai irin yadda lips ɗin jarirai yake sheƙi in sun ɗan laso lips ɗin. Wata tattausar jallabiya blue color mai ɗan karen taushi da kyau ne, a jikinsa, tayi cib-cib da ɗan madaidaicin jikinsa, sai kuma fararen takalma half cover masu taushi da ya zira tattausan sawayensa da suke farare ƙal, yayinda dun-duniyar sawun nasa ke sarari. Farin hirami ya naɗa a kansa, irin naɗin nan na zamani wanda matasan larabawa keyi, Sai wayarshi daya zira a ajihun gaban jallabiyar tasa, wani irin sassayan ƙamshi mai ɗan karen daɗin shaƙa yake zubawa, Taku yakeyi cike da kamala, yayinda hannunsa na dama ke riƙe da jakar system nasa. Cikin yanayinsa na nitsuwa ya ƙara so bakin kitchen ɗin. Siraran Idanunsa ya ɗan jujjuya ya kalli tsakiyar gidan baki ɗaya, sai ya kuma ɗan leƙa cikin kitchen din, nan ma babu alamun Innayi. Cikin nitsuwa ya kuma juyowa ya nufi ɗakin nata, ganin takalmanta a bakin ƙofar. “Assalamu alaikum”. Yayi sallama cikin wata iriyar sassayar muryar mai cike da haiba nitsuwa da kamala. Sai kuma yayi saurin shigowa cikin ɗakin. Ganin Innayi na kwance bisa sallaya babu ko pillown ga kuma karkarwa da jikinta keyi. A hankali ya rusuna tare da takwara ƙafarsa ta dama ya zauna kanta ta hagu kuma ya tsaidata, cikin kulawa da tarin so tausayi, ya motsa lips ɗinshi a hankali yace. “Yah Salam. Innayi! Innayi!! Innayi!!!”. Ya kirata sau uku, ganin bata amsa bane, yasashi manna tafin hannunsa kan goshinta, wanda hakan ne yasata buɗe kwayar idanunta da sukayi ja. Sai kuma ta medasu ta rufesu, sai ga wasu hawayen masu zafi sun kwaranyo mata. Jiki na rawa tasa hannunta, ta kamo hannunsa, murya a raunace tace. “Aliyu”. Da sauri ya zuba mata idanun tare da tsareta dasu, domin zai iya cewa, wannan shine karo na biyu a rayuwarsa da yaji ta kirasa da asalin sunansa na yanka. A hankali yace. “Na'am Innayi meke damunki? Meyasa baki kirani kin gaya min baki da lfy ba? Tashi mu tafi asibiti”. Ya ƙare mgnar yana mai tallabota ya zaunar da ita. Wani dogon numfashi Innayin taja cikin rawan murya tace. “Aliyu ka zauna, kaji abinda zan gaya maka”. cikin yanayin kulawa a sanyaye yace. “A'a muje asibiti tukuna, sai mun dawo”. Cikin ɗan ɗaga murya tace. “Aliyu ka bari kaji abinda baka saniba. Bana son in mutu in barka a nahiyar maraici, bana son in mutu da abinda ni kaɗaice na sani kuma nakeda dama da ikon sanar da kai, idan na mutu a haka ban sanar da kai abinda ke bibiye da muba, nayi maka cuta mafi muni a rayuwarka. Aliyu ka bari in sanar da kai abinda Allah ya nuna min a daren jiya”. A hankali ya fesar da nannauyan numfashi, sai kuma ya juyo ya kalli ƙofar ɗakin, jiyo Muryar Amininsa mafi ɗan uwa, wato M Jamil yanayin sallama, a hankali yace. “Wa alaikassalam J”. Ya ƙira Aminin nasa da sunan da duk duniya shi kadai ke kiransa da hakan, Ido ya zubawa M Jamil ɗin a hankali tare dayi masa alamun ya shigo da kwayar idanunsa, Cikin yanayin sauƙin kai sakin fuska faram-faram Jamil ya sako kansa cikin ɗakin yana mai cewa. “Iya innare yau me kika dafa mana ne, dan tun jiya da na dawo ƙasar nan banci komai ba, nace sai abincinki zanci ko na Ummina”. Sai kuma yayi shiru tare da matsowa kusa da ita... Cikin Masarautar Gembilan kuwa. Wata Kekkyawar matace yar duma-duma mai kyan shiga da haiba, ke zaune bisa kujera, yayinda System ke gabanta bisa ɗan madaidaicin stool yayinda fuskarta ke manne da wani ɗan farin glass siriri. Da alamu typing takeyi. Kai ta ɗan jinjina tare da juyowa ta kalli dinning area inda hayaniyar yaranta ke tashi. Kai ta ɗan jinjina tare da kallon wata yar narkekkiyar matashiya da bazata wuce 14 year's ba. Ido ta zuba mata ganin ta nufota da sauri. Hannunta ɗaya. Riƙe da school bag da takalmin sinika da kuma ɗan madaidacin hijabin Uniform ɗin ta. Da sauri ta rusuna gaban Matar tare da juya mata baya tana cewa. “Ayya Momy tubke min kaina, nayi-nayi yaƙi sai na ƙulleshi sai ya sule”. Kwaffa tayi tare da cewa. “To wai ke kam Khausar yaushe ne zaki iya, tubke gashin kanki”. Ta ƙare mgnar tana tattaro suman Khausar din yana mai zamewa, Sai kuma ta ɗago kanta ta kalli Ɗan matashin yaron da yanzu ya fito cikin Uniform ɗinsa. Wanda yake iri ɗaya dana jikin wacce aka kira da Khausar. Da alamun ya gama shirinsa tsab. Cikin tsuke fuska ya watsawa Khausar din harara tare da cewa. “Gsky ni zan tafi Ramadan Raudat zomu tafi, kullum ita ke jaza mana yin letting muje aita zanemu kamar bayi. Ni wlh da zan samu a rabamun hanya da ita inaso, muna shiga school kamar wasu shaidanu zakaji an fara cewa. FATTANAH kuka biyewa ko, duk sai an gama shiga aji kafin ku iso.” Cikin yanayin tsiwa da son girma ta miƙe tsaye tana ɗaure ɗan kwalinta harara ta watsa mishi tare da cewa. “Wallahi ka shiga hankalinka dani Haydar in baka dena cemin FATTANAH ba zan fasa maka baki”. Dogon tsaki yaja tare da juyawa ya nufi ƙofar falon, yana gyara zaman net ɗin sa. Tare da cewa. “Sai ki gayawa wanda yasa miki sunan, ko kuma ki nitsu ki dena rashin kunya da rawan kai”. Cikin ɗan ɗaga murya Momyn nasu tace. “Gsky Babana bana son wannan sunan da aka liƙawa Mamana sam bafana son sunan”. Da sauri yace. “Toh Momy ai ita ta jawa kanta fitinenneyar ce ta gasken gaske, in dai kinji faɗa to da ita a ciki, in kuma babu ita to zakiji ance ai gulma akayi ta maidawa maishi, wai ita ba'a gulma da ita, itafa tana iya zuwa zuwa ta samu ana faɗa ta shiga tayi kane-kane sai an gama tace wai me dalilin faɗan”. Ya ƙare mgnar yana fita. Ita kuwa Khausar zama tayi gefen Momynsu tana sa takalmanta da ɗan sassarfa domin yau din ranace ta musamman a wurinta tana cike da ɗokin zuwa makaranta kasancewar yau suka dawo hutu, kuma hutune na canjaza aji da JSS zata tafi SS 1 wanda takega matakin samun encinta ne kenan zata taka, tunda yanzu zata koma aji da matan aure, a islamiyar safe, sai kuma na bokone tacan anan ne babu enci sai randa ta gama sa takalmin ta saka, tana sakin yelwataccen murmushi. Yayinda Ramadan da Raudat suke tsaye gefenta. Hannu tasa ta kama hannun Raudat tare da cewa. “Mu tafi”. Da sauri ta juyo ta kalli Momyn nasu tare da kwaɓe fuska jin tana cewa. “Ku biya sashin Gimbiya Dadu ku gaidata, bata da lfy”. Cikin kwaɓe fuska tace. “Momy zamuyi letti muje wannan mai sunan baban naki ya samu damar sawa a azabtar dani”. Ta ƙare mgnar cikin son zillewa zuwa sashin Gimbiya Duda, ita kuwa Momy tsuke fuska tayi tare da cewa. “Ku biya ku gaisheta da jiki nace ko”. Cikin bin umarnin mahaifiyar tata badon tasowa tace. “Toh Momy”. Daga nan ta kada kan ƙannen nata Duk suka fito. Sai kuma tayi sauri ta juyo tare da cewa. “Momy mun tafi”. Murmushi tayi sanin manufar ta yasa cikin lumshe idanu tace. “Allah ya kaiku lfy ya baku Sa'a Allah yasa ki shiga SS 1 da ƙafar dama, Allah ya shirya min ku”. Cike da jin daɗi tace. “Amin Ya Allah”. Kana suka fita. Suna fitowa suka samu duk sauran yaran gidanma sun fito. Kamar haɗin baki kab ɗin su sashin Gimbiya Dadu suka nufa. Kai tsaye suka wuce har bedroom ɗin ta domin bata falon. Su Asiya ce, a gaba ita da sauran ƙannenta, sai kuma su Khausar din. Zaune suka sameta bisa tsakiyar gadon mulkinta, mai martaba Lamido Gembilan yana zaune ƙasa bisa carpet, yana haɗa mata tea, Cikin tarin biyayya, da sauri suka rusuna baki ɗayansu, kusa haɗa baki sukayi wurin cewa. (“Allah saine Abba, noi nɓanɗu Dadu?) Allah ya faranta maka Abba ya jikin Dadu?”. Cikin son ahlin nasa ya jinjina masu kai tare da cewa. (“Yettore Allah nwodi dama) an godewa Allah da sauƙi”. “Allah ntokkin dama”. Suka faɗa a tare, cikin tankwashe sawunsa yace. “Allah jabu”. Amin suka faɗi baki ɗayansu, Yayinda Khausar kuma taketa jan hijabinta, tana mai sunkuyar da kanta ƙasa, Allah ya sani bata ƙaunar abinda zai kawo ta gaban Gimbiya Dadu, Domin jikinta da nitsuwarta duk rasasu takeyi, sabida wani irin mayataccen kallo mai bada tsoro da tsohuwar ke Binta dashi. Kamar koda yaushe kuma hakane, duk da bata da lafiya, amman wani irin masifeffen kallo ta tsare Khausar ɗin dashi har bata jin gaisuwar da jikokin nata keyi mata, Cikin taɓe baki Asiya tace. “Dadu wannan wanne irin kallo ne? muna gaidaki kinyi shiru?”. Jin hakanne yasa Khausar ɗan ɗago kanta, Ai kuwa ido cikin ido sukayi da Dadu. Da sauri ta motsa lips ɗin ta a hankali tare da cewa. “Innalillahi wa innailaihi raji'un”. Sabida wani irin tashi da tsikar jikinta ya farayi, yam-yam. Ita kuwa Dadu har lau bata cire idanunta a kantaba, Haydar ne ya ɗan miƙa tsaye tare da kamo hannun Ramadan da Raudat yace. “Dadu Allah ya sauwaƙa, zamu tafi school kada muyi letti Raudat muje”. Abin mamaki har lau Dadu batama san anayi mata mgna ba, bare ta amsa musu, gaba ɗaya nitsuwarta da kallonta yana kan Khausar....! Lamido kuwa ido ya zubawa maifiyar tasa, cike da mamakin lamarinta, ya zama ana kallon kalo, ita tana kallon Khausar data kasa koda ƙwaƙƙwaran motsi shi kuwa yana kallonta. Asiya kuwa itama miƙeqa tayi tare da kaɗa kan ƙannenta tayi gaba Amina ce ƙanwar Asiya mai binta ta ɗan miƙa tare da cewa, “Uhum”. ta fice Ya zama daga Dadu sai Lamido sai Khausar. Cikin wani irin yanayi da Khausar din keji ta kuma kallon Dadu, wacce zuwa yanzu ta saki laɓen bakinta na ƙasa, wani irin yawu mai cike da mayataccen kwaɗayi ne ya tsinko mata, har yana ɗan sauƙowa kan lips ɗin ta. Cikin sauri Khausar ta miƙe jin Lamido yana cewa. “Mamana tashi ku tafi”. Ai kafin ma ya rufe bakinsa, tuni ta fita tana mai cewa. “Toh Abba”. Ita kuwa Dadu wani nannauyan numfashin ta sauƙe tare da juyowa takalli ɗan nata, dake miƙa mata cup ɗin tea. Cikin diriricewa tace. “A'a bana buƙatar abin zaƙi, a kawo min abu mai yaji-yaji”. Cike da biyayya yace. “Toh”. Kana ya miƙe ya fita. Tuni su Khausar kuwa sun shiga school bos ɗinsu, Amina ce ƙanwar Asiya mai binta ta kalli Ramadan dake cewa. “Kalli fa 8:13 na tabbatar yauma zamu zanu”. Cikin sanyi tace. “Mu dai Allah ya rufa mana asiri daga SS 2 akwai matan aure da yawa a ciki, so ba batun duka a side ɗin mu. Kuma ma duk bama saɓa doka cikin nitsuwa da tarbiyyar mu muke, ko nayi litting nasan za'ayi min uzuri. Cike da jin daɗi, Khausar tace. “Nima dai Allah ya yaye min masifa da cin zalin su Moddibo tunda yau dai zan tafi Ss 1 ɗin, da ba duka ba zagi, wlh inci karena babu babbaka”. Taɓe baki Haydar yayi tare da cewa. “Mu gefen maza, babu manya, duk yarane, manyan da dare suke zuwa, shiyasa babu roggomi”. Asiya ce ta kalli Khausar cikin yanayin son yarinyar tare da cewa. “Ai wlh ke dai in baki nitsuwa ba ko jami'a kikaje in dai Moddibo na cikin malamanku, na tabbatar zai san matakin da zai ɗauka a kanki. Sannan ma da kike batun kin tafi Ss1 akwai matan aure, kin mance cewa, na safene, na islami. Akwai na rana zuwa biyar bokone, kuma kuna tare da moddibo.” Kwaffa tayi tare da cewa. “Kai na shiga ukuna wlh”.. Anan gefen su Modibbo ku, fir innayi taki aje asibitin. Su kuna su kasa fahimtar ta, gani suke zafin zazzaɓin maleria ne yake son sata surutai shiyasa suke hanata mgn sukayi ta mata addu'o'i hardai ta ɗan fara samun nitsuwa har bacci ya ɗan sureta. Gani ta ɗan rumtsane yasa suka tafi wurin Ummin M Jameel suka ɗauko Ummin dan tazo ta ɗan kula da ita. Suna isa bakin gate, ba tare da sun shigaba, Ummin ta kalli M Jamil da yayi saurin fitowa bayan yayi parking marfin motar ya buɗe, mata cikin tsananin son mahaifiyar tasa, yace. “Bismillah Ummi fito ki shiga wurin Innayinki, domin mu dai yau mun gaza gane kanta, da alamun Ita dai dare ɗaya gigin tsufa ya sauƙo mata”. Ɗan buge ƙeyarsa tayi tare da ciwa. “Tsufa kan zai cimma taka uwar mafa, kawai dai inaga zafin zazzaɓine kusan wasu lokutan yanasa yara surutai, to ita kuma girma yazo dole in ciwon yayi zafi zatayi kamar na yara”. Juyowa tayi ta kalli Moddibo daya jingina kansa jikin kujerar gaban motar gefen mai zaman banza, Cikin sanyin murya yace. “Uhmmmm Ummi waifa cewa tai taga taurari suna sauƙowa ƙasa har kamar zasu taɓa rufin side nan, anya kuwa Ummi wannan zazzaɓi ne?”. Sai kuma ya ɗan fesar da numfashi tare da lumshe idanunsa cikin alamun nazari yace. “Ina tsoron kada fa matsalar ƙwaƙwalwa ce, nayi nayi muje asibiti kuma taƙi.” Ya dire mgn tare haɗa kan yatsun hannunsa. Jamil ne yaci gaba da cewa. “Saida fa Moddibo yayi ta mata tofi kafin muka samu tayi bacci har muka fito ɗin.” Cikin kulawa Ummi tace. “In sha Allah babu komai, bari in shiga, ku kuje”. To Jamil yace kana ya shiga mota, ita kuma tayi cikin gidan. A hankali ya miƙa dalleliyar motarsa ƙirar BMW kan shimfiɗeɗen titin, Yana tafiyar hawainiya, murmushin yayi ganin kallon da Moddibo yake masa. “Sanin yau za'a dawo makaranta ne, yasa nayi ƙoƙarin dawowa baro Marrocco, duk da akwai ayyukan da ban gama dasu a company'nba,”. Cewar M Jamil shi kuwa Moddibo kai ya jinjina alamun yana jinsa, shi kuwa M Jamil gudu ya ɗan ƙara tare da ci gaba da mgn dan yasan ba lallai ne Moddibo ya amsa mishi da bakiba, inda sabo ya saba, kuma shi yasan cewa body language al'adane ko ɗabi'a koma yace halittar Moddibo ne. Juyowa yayi ya kalleshi tare da cewa. “Na zaƙu muje makarantar nan, dan nasan zaiyi kyau sosai a tsarin gyarashi da akayi”. Cikin ɗan ƙwaɓe fuska yace. “In an gama gyaran ba”. Da sauri M Jamil yace. “Kamar yaya za'a gama mana”. Juyowa yayi ya ɗan kalli M Jamil ta gefen ido kana a takaice yace. “Toh ba'a gaman ba”. Cikin sauri M Jamil yace. “A.S da gaske ba'a gama ba?”. A.S shine sunan da yake kiran Moddibo dashi kuma su biyu kaɗai suka san ma'anar sai kuma abokan karatunsu. Shi kuwa Modibbo littafin dake gaban motar ya ɗauka tare da buɗe wa kana yace. “Dama tun lokacin da za'a bada hutun na faɗa bazai isa a gama gyaran school ɗin ba, musamman da ya zama an ƙara yawan class, kana ga gina hall din da akace za'ayi, kuma dole aikin bazaiyi guduba sabida Ramadan, tun lokacin nace a ƙara kwanakin hutun, sabida samun isasshen lokacin, wannan Ba fulatanin yaƙi”. Murmushin M Jamil yayi tare da cewa. “Toh kai meyasa baka ƙara hutunba, ai da sai ka sanar”. Juyowa yayi ya kalleshi bayan hannunsa yasa ya shafa tattausan sajensa tare da cewa. “Uhmmmm”. Ya san me wannan Uhmmm ɗin take nufi, kai ya jinjina tare da cewa, “Mu dai yan kallone,". Da sauri yace. “Nima haka, dan na gaji ko yaushe sai ya kwaɓa abu yazo yana cemin ina mafita”. Dai-dai lokacin aka buɗe musu gate din makarantar, Ya Salam. Wani irin tsarine da zubi makarantar yake dashi, tsari mai burgewa, yayinda shima makarantar Moddibo ya ƙawatata da tsirrai na kyautata muhalli. Tabbas gyara kam da saura ba'a gama shi ba. Domin daga woje dai kam an kammala komai amman daga ciki, duk cikin ajujuwan a hargitse yake. M Jamil nayin parking, wani kekkyawan dattijo bafulatani ya nufo matar tasu da sauri, bisa alamu dai shine shugaban makarantar domin duk malaman na miƙa gaisuwar garesa cikin mutuntawa. “Moddibo! Moddibo!! Moddibo!!!.” Jamil ne ya fito yana murmushin tare da cewa. “Allah rene,”. Da sauri yace. “Ina Moddibo”. Cikin motar Jamil ya nuna masa, da sauri ya sunkuyo, Yayinda shi kuwa Moddibo meda bayansa yayi ya jingina tare da lumshe idanunsa, murmushi Dattijon yayi tare da cewa. “Ga ɗalibai duk sun dawo makaranta ta cika maƙil ga sabbin ɗauka, kuma aiki baifi rabi ba, ya zamuyi?”. Cikin taɓe baki yace. “Allahu a'lamu!”. Jamil ne ya juyo ya kalli Malam Ahmad da Malam Habibullah da suma fitowar su kenan daga can cikin makarantar. Shi kuwa Malam Arɗo Umaru mamallakin makarantar kuma . Kai ya ɗan dafe tare da cewa. “Dan Allah ka fito Moddibo kasan bayanin da zakayi musu, kana ka kara musu kwanakin hutun, tsawon lokacin da kakega za'a iya gama gyaran”. Yadda ya dire mgnar da karya wuyane yasa Moddibo fitowa. Murmushin sauran malaman sukayi, domin sosai tsufa ya fara cimma Mala Arɗo, zuwa yanzu ya kamata ragamar makarantar ya zama a hannun yara, domin badon Allah yasa Moddibo ke tsara komai na jadawalin abubuwan ciki da wajen makarantar ba, da tuni ta durƙushe, to amman sabida shi da sauran haziƙan malamai da suke da tsananin kula da tarbiyyar yara da sukeyi yasa har yau makarantar bata da na biyu a faɗin birnin Gembila. Kusan a tare suka rakaya cikin makarantar. Yayinda hayanin ɗalibai manya da yara maza da mata, ke tashi. Juyowa yayi ya kalli Jamil tare da cewa. “J kaje masallaci kayi mgn duk mu su haɗu a tsohon halla ɗin mu na sama.”. To Jamil yace yana tunanin to me zaice musu, Masallacin ya wuce tare da yin sanarwan. Nan take kuwa, duk ɗaliban suka haura sama, suka shiga cikin babban hall ɗin nasu wanda yake ƙato sai dai duk da haka yanzu ya musu ƙaramin,. A gafen mazama suma duk sun haɗu a halla nasu. Shi kuwa Moddibo office nasa ya wuce. Jim kaɗan ya fito, da Lapel Microphone a hannunsa yana saƙalasa a wuyan tattausan jallabiyar jikinsa Malam Ahmad ne ya matso kusa dashi tare da cewa. “Zamu jirane ko an ƙara mana hutu”. Ɗan murmushin gefen baki yayi tare da cewa. “Hutu kuwa sosai ma har na tsawon mako uku za'a ƙara”. Cike da murmushi yace. “Mu tafi kenan”. Kai ya gyaɗa masa tare da cewa. “Suma duk yanzu zan kaɗa kansu ko wacce tai gida sai dai muma muna da zama na musamman”. Ai kuwa jin haka yasa duk malam suka zauna jiran. Shi kuwa ya haura saman yana mgn da M Jamil a waya. “Su maza basu da hayaniya, kawai J ka ɗanyi musu nasiha, kana kace sai bayan mako uku zasu dawo kafin nan an gama gyara, Sai dai masu zuwa hadda suci gaba da zuwa." Cike da gamsuwa M Jamil yace to. Kana sukayi sallama. Dai-dai lokacin kuma su Khausar suka shiga cikin makarantar, Da in ka gani kace a ƙasashen ƙetarene, domin makaranta ce mai zaman kanta, mai cike da haziƙan malamai, duk da sunyi makarar mintuna 20, an bar motarsu ta shiga ne, sabida magiyar da sukayi tayi da kuma girman gidan da suka fito, da bada uzurin motar ta ɗan lalacemusu a hanyane kana da kuma ganin ma yau ba karatun za'ayi ba, hutun za'a kuma ruɓanyawa. Suna shiga kuwa, ga mamaki su aka barsu suka shige ba hukuncin komai. Kana ko wa ya nufi sashin da ajinsa yake. Da sauri duk suka tsaya jin Malam Habibullah na cewa. “Fattanah uwar yan letti yau makarar har ta 20 minute duk da yau aka dawo, duk kuyi sama ana taro a hall”. Cikin ɗan tura baki tace. “Toh Malam”. Yayinda tuni su Asiya kam sun haura har sun shiga hall ɗin. Da ɗan sassarfa ta fara take steps ɗin da zai sasanta, da hall da yake a sama ganin ita kaɗai ta rage. Daga corridor'n steps ɗin, ta ɗan lumshe idanu ta, tare da gyara saƙala school bag ɗinta a kafaɗar dama. Sabida ƙamshin turarensa ya shaida mata, tabbas tuni ya shiga hall ɗin. A hankali ta sauƙe numfashin ta tare, da nemo dukkan nitsuwarta. Lokacin da ta gama haurowa, sama, da sauri ta tsaya, jikin window dake gab da bakin ƙofar shiga, ido ta lumshe tare da buɗewa a hankali kana ta kutsa kai cikin hall din da a kalla mutane ciki sun kai ɗari da hamsin, duk da tasan bai taɓa barinta, ta shiga ajiba, muddin ya rigata shiga, to amman kullum sai ta gwada sa'anta musamman yau da yake a hall ne. Taku ɗaya tayi ana biyu, ta tsaya, sabida, ganin ya ɗaga mata, tafin hannunsa. Cikin yin mui-mui da bakinta tace. “Afwan ya mu'allim sayyara...”. Da sauri ta ɗan ja da baya ta koma jikin window ganin ya juya baya tare, da gyara ɗan masaƙalin Lapel Microphone dayake saƙale a wuyan jallabiyar jikinsa, sabida tsananin sanyin sautin muryarsa yasa dole sai dashi yake amfani a cikin class, domin ɗalibansa su samu damar jinsa sautinsa ras domin sam baya iya kware muryarsa yayi mgna da ƙarfi haka Allah ya haliccesa da nitsestsiyar sauti to bare a irin taron maƙil da hall ɗin yayi yau. Cikin tattausar muryar sa mai cike da sanyi yace. “Makfut?”. Cike da jin daɗin nasihar da yakeyi musu suka amsa da “Na'am”. Kai ya jinjina tare da cewa. “Ɗeyib!”. Sai kuma ya ɗan juyo ya fuskancesu, hakan ya zama, ya ɗan bawa Khausar baya, tattausan sumar ƙeyansa dake kwance lib-lib ta zubawa harara. Numfashi mai sanyi taja tare da shaƙa daddaɗan ƙamshin turarensa mai sawa ɗan adam salama. Sai kuma tayi ƙasa da kwayar idanunta dugadigin sawunsa, ta zubawa idanu tana ganin yadda sukeyin ja in ya taka sawun, in kuma ya ɗaga sai suyi fari, baki ta ɗan tura sama ta da liƙa ƙeyarshi wani sabon hararan. Shi kuwa Moddibo a hankali yake taku a gaban ɗaliban nasa, masu biyayya da girmamawa a garesa, cikin tattausan lafazi yace. “Falalar zikirai da karatun Alqur'ani , nakeso son in tunasar mana, sabida kididdigar manazarta, ta nuna mana Al'ummar wannan ƙarnin sun samu naƙasun zikiri da karatun Alqur'ani mai girma, sun maida hankali akan sashin yanar Gizo-gizo fiye da yadda ya kamata, mu maida hankali kan Al'ƙurani littafin Allah da hadisan Manzon Allah, mu samman a wannan taki da muke ciki, na shuɗewar Ramadan wanda zaka samu da yawa mutane sun fuskanci aikin al'khairai da bautar ubangiji a cikin watan, da zaran watan ta gabata sai a koma gidan jiya aita sharholiyar duniya.” Sai kuma yayi shiru, tare da fesar da numfashi a hankali, kana ya juyo a hankali yace. “Mutane da yawa sun mance koma ince wasu basu san me Allah maɗaukakin sarki yace ba A cikin Suratul Baqara, ayata 152. Allah maɗaukakin sarki yace. فَاذْكُرُونِي أَذْكُرْكُمْ وَاشْكُرُوا لِي وَلَا تَكْفُرُونِ. Ma'ana: Ku ambaceni zan ambaceku, ku godemin kada ku butulcemin.”. Ya ƙare mgnar da rumtse tafin hannunsa alamun ƙarfafa mgnar, wanda kuma wannan ɗabi'arsace ko ace halittar sace. Duk mgnar da yakeyi yana kamantata ko suffantata da tafukan hannunsa like dai yadda manyan sarakuna keyin mgn turawa kuma suka cewa hakan body language, Wanda mafi akasari ɗabi'ar yan jarida ne, in suna mgn. Shiru hall ɗin yayi alamun suna fahimta sosai. Shi kuwa Moddibo cikin girmama zancen Allah madaukakin sarki yaci gaba da cewa. “A dai wannan ƙarni da muke ciki da yawa, suna butulcewa faɗin Allah madaukakin sarki, daga barin ambatonsa, gaba ɗaya shagala tayiwa al'ummar mu ƙawanya, shafukan sada zumunta na yanar Gizo-gizo ya maiye gurbin da yake muhallin Qura'ani ne a wurin wasu musul manmu, sai a wuni a kwana musulmi bai ɗauki Qura'an ya karanta ya duba kyan baƙin da yake haɗawaba, amman sai ka sameshi awa 14 na awannin 24 na rana yana rungume da wayarsa, ana charting, a Facebook a koma whatsApp, daga nan a tafi Instagram, sai kuma a murgina a koma twitter sai kuma a rarrafawa zuwa wannan lalataccen kuma kazamin dandalin Tiktok, ayi ta raye-raye da waƙe-waƙe, anaiwa juna cin zarafi, wasu su koma yiwa malamai isgilanci ana yaɗa fasadi da fajirci ana meda ashariya kamar ruwan sha.” Ya dire ayar mgnar tare da haɗe kan yatsun hannunsa gaba ɗayansu wuri ɗaya alamun ya dunƙule mgnar kenan bawai ya gamata bane zai tafi sashi mafi muhimmanci ne. A jikin window a waje kuwa, cikin jujjuya ido Khausar ta raɓa jikin window tare da maida hankalinta baki daya cikin. Shi kuwa Moddibo a hankali ya ɗan juyo gefen damansa, jin inda sautin surutu yake ɗan tashi kaɗan. Ganin yana kallon sune kuwa yasa, Samira Sani yin shiru. Cikin nitsu ya kuma cewa. “A wata ayar kuwa a cikin suratul Ahzab ayata 41, me Allah maɗaukakin sarki yace mana!???”. Ya ƙare mgnar da alamun ayar tambaya, hakan na nufin su ja mishi baƙi yake so, sanin mafiya akasarinsu yan haddansa ne, Ji kakeyi, hall din sit kowacce tayi ƙasa da kai, gudun kada ya nuna ta kaɗan daga cikinsu kuma bawai basu sani bane diricewa ne da kwarjininsa ke sasu yin ƙasa da kai. Cikin sanyi yace. “Na'am Samira Sani”. Da sauri tace. “Malam ni?”. Fuskarsa ya tsuke tare da juyowa ya kalli Asma'u Ahmad dayi mata alama da hannu, tsilli-tsilli tayi da idanu. Samira Sani kuwa ganin ya cire ido a kanta ne yasa tayi saurin buɗe Qura'an ɗin ta. Dan dubo ayar, sai kuma duk suka ɗago kansu suka zuwa Khausar dake jikin window idanu, jin ta uzi shaitan tare da yin basmalla kana taja numfashinta tare da lumshe idanu murya cike da tajwed ta fara jan ayar. Surah Al-Ahzab aya ta 41: يَا أَيُّهَا الَّذِينَ آمَنُوا اذْكُرُوا اللَّهَ ذِكْرًا كَثِيرًا Murmushin mai cike da jin dadin Asma'u Ahmad tayi tare da sauƙe numfashin, FATTANAH ta ɗauki belinsu kamar yadda aka saba, domin in dai batun jane na ƙwaƙwalwa to kwanyar Khausar ta musamman ce. Mata da yawa kuma cikin manyan mata kallonta sukeyi cike da sha'awa da jin daɗin zazzaƙar muryarta na kuma ratsa musu kunnuwa. Shi kuwa Moddibo ba tare da ya juyo ya kalle taba. Ya fara kawo musu fassarar ayar. “Allah madaukakin sarki yana cewa: Yaku waɗanda suka yi imani, ku ambaci Allah ambato mai yawa. Ammato kuma na haƙiƙa bawai kawai kije kiyi karatun Qura'an kara zube ko gatsa-gatsa ba, kuyi karatu kwatankwacin yadda tayi inma kunce juyawa ih zuwa irin nawa da wuya.” Cikin sanyi Asma'u Ahmad tace. “Malam ai karatun Khausar irin nakane, ba banbanci kawai dai, ita muryar mata kai muryar maza muna son mu koya irin ƙira'ar sosai.” Kai ya ɗan juya ya ɗan basu baya tare cewa. “In sha Allah zaku iya”. Samira Sani kuwa, tattausar sajensa ta zubawa idanu cikin wani irin salo dake cikin jiki da zuciyarta. Shi kuwa Moddibo a hankali ya kuma yin gyaran murya tare da cewa. “A wata ayar kuwa cikin suratul A'araf aya ta 205. Allah maɗaukakin sarki na cewa... Sai kuma yayi musu alamun suja ƙira'arar. Cikin kauda kai Khausar ta lumshe idanu ganin wani irin masifeffen kallon daya watsa mata, wanda saida taji hantar cikinta ta kaɗa. Cike da dagiya a fagen neman ilinta dan bata wasa kuma bata barin tsoronsa ya hanata fahimta, cikin nitsuwar da take samu in zatayi karatu tayi bismilla tare da fara jan ayar. “Surah Al-Araf, aya ta 205: وَاذْكُر رَّبَّكَ فِي نَفْسِكَ تَضَرُّعًا وَخِيفَةً وَدُونَ الْجَهْرِ مِنَ الْقَوْلِ بِالْغُدُوِّ وَالْآصَالِ وَلَا تَكُن مِّنَ الْغَافِلِينَ Ta dire ayar da sauƙe nannauyan numfashi sabida tagib da taja, wanda dole ta ɗan riƙe numfashinta na kusan second 32. Samira kuwa, wani irin malolon bakin cikine, ya tokare mata maƙoshi, sabida masifar kishi da takaicin yadda ko yaushe Khausar ke gaba dasu. Asma'u kuwa sai murmushi takeyi, Yayinda da yawa suke fatan Allah ya buɗa musu kwakwalensu kamar na Khausar. Shi kuwa Moddibo a hankali ya fara fassara musu ayar. “Abinda Allah madaukakin sarki yake cewa. (Kuma ka ambaci Ubangijinka, a cikin zuciyarka, kana mai ƙanƙan da kai, da tsoro, ba da ɗaukaka murya a, tsaka-tsaki tsakanin asirtawa da bayyanawa da safe da kuma maraici, kuma kada ka zamo cikin falaki,. A wata ayar kuwa, Allah madaukakin sarki na cewa. (Da masu ambaton Allah, maza, da masu ambaton sa mata, Allah ya tanadar musu gafara da lada mai girma)”. Sai ya kuma ɗan tsagaita wa tare da kallonsu yana cewa. “Makfut?”. “Na'am”. Suka amsa baki ɗaya, “Ɗayyit”. Yace tare da kallon agogon hannunsa, ganin saura 9 minute lokacin da ya kamata ya sallamesu yacika ne, yasashi ci gaba da cewa “Kuma Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi yace: (Misalin wanda yake ambaton Allah da wanda baya ambaton Ubangijinsa kamar misalin rayayya ne da matacce. A wani wurin kuma yace. (Shin bana baku labarin mafi al'khairin ayyuka ba, kuma mafi tsarkinsu a wajen Sarkin da yake mallakarku, kuma mafi ɗaukakarsu, ga darajojinku, kuma mafi al'khairi gareku daga ciyar da zinariya da azurfa, kuma mafi al'khairi gareku daku haɗu da abokan gabanku ku riƙe dukkan wuyoyinsu kuna dukan wuyoyin suba?) Duba Sahihul Bukhari, tare da sharhinsa Fathul Bari (11/208) Muslim ya ruwaito da lafazin: Misalin gidan da ake ambaton Allah a cikinsa da wanda ba'a ambaton Allah a cikinsa kamar misalin rayayya ne da matacce, (1/539) Sai Sahabbai Sukace ka bamu labari. Sai yace musu. (Ambaton Allah madaukaki sarki) Kuma yace: Allah madaukaki yana cewa: (Ni ina tare da zaton bawana dani, Kuma ina tare dashi idan ya ambaceni, cikin ransa, zan ambaceshi a cikin raina, Idan kuma ya ambaceni a cikin jama'a zan ambaceshi a cikin jama'ar da ta fisu al'khairi, in ya kusanceni taƙi ɗaya, zan kusancesa kamu guda, in ya kusanceni kamu guda, zan kusancesa tsawon gaɓa guda, in yazo min yana tafiya zan zo masa ina gaggawa)”. Sai kuma ya fesar da sassayan numfashi a hankali tare dasa tafin hannunsa ya shafa tattausan sajensa, yana mai lumshe idanunsa alamun cikekkiyar nitsuwarsa buɗe idanun yayi a hankali tare da cewa. Tirmizi (5/459). da Ibn Majah, (2/1245). duba Sahih Ibn Majah (2/316). da kuma Sahihul Tirmizi (3/139). Bukhari (8/171). Da Muslim (4/2061) lafazin riwayar na Bukhari ne. Cikin nitsuwa ya kuma juyowa ya fuskacesu, murya cike da kamala, da tashin lafazi yace....! *WOHOHO IN KAJI ANA ƘI GUDU TABBAS SA GUDU NE BEZO BA* _Ina kuke Ma'aurata masu sha'awar ganin sun zama taurari kuma fitilu a idanun mazajensu Uwar gida,Amarya,Tsakar gida,hadda tan kaɗen gida Shararriya kuma ƙasaitacciya data saba kawo muku nau'ikan sirrin sahihan magungunan ma'aurata wato *AYSHA ALIYU GARKUWA* Garkuwar Marubuta ayau ma na dawo muku da Ingantattun magungunan mata masu kyau da inganci domin gyara kanki ki zamto tauraruwa a idanun mijinki...Muna da Ingantattun Abubuwa kamar haka_ :_Munada Garin mallaka, garin maɗi, garin Hakkin mayi, garin ɓelɗamhi Garin ilanwaddihi, Gumbar da ba'a baiwa mai kishiya, Gumbar kolli mai kellin al'khairi, Gumbar Riɗi wato 3 in 1, Gumbar makwaranyi Gumbar Ukku al'khairi, Dukansu garukan da gumbunan akan dubu uku uku ne sai gumbar Riɗi da uku khairi su dubu biyar biyar ne ! Masin Maliƙi mai masifar ƙarfi da matse mace ta koma tamkar budurwa 7k, kana masin Daɗi har Maɗigan mai masifar kyau da kwaranyo da ni'ina 5k Akwai, kwanon ƙasaitacciyar mace mai masifar kyau da ratsa jiki da samar da inƙantacciyar ni'ima yanada abubuwa masu kyau haɗinsa 8k, Zumar goron tula mai masifar kyau, tsumin dabino, mai ratsa jiki, tsumin Riɗi mai ƙarfi, Furar Mata mai tsastsafo da ni'imantaccen damshi duka a dubu uku-uku ne ƙananan robobinfa, Cida kaza, Ciccibi Abodi, Tsumin Ɓaure, tuwon ɓauren, kana akwai maganin sanyi sadidan, set dinsa dubu goma in kuma komai rabi-razi zan sa miki 5k ne butar sirri da dai sauransu...Se kuma fannin ƙamshi kasance da Shu'umin ƙamshi wanda ze gigita ƙwaƙwalwar Oga tare da jin ko wacce mace bata kaiba...._ _Shin ko kina da labarin Miskilinci da ƙasaitar Rayyan Naaan amma lokaci ɗaya ya zamto zautacce sakali akan soyayyar Jannart bakomai Jannart ta riƙe ba face sirrinkan gyara da kuma shu'uman humran da kulaccar sirri na Aysha Aliyu Garkuwa(Tubali) tabbas taga tasirin haka domin Naanunta ya zame mata tamkar bawa_ _Shin ko kinsan sihirtaccen haɗin da Aysha ke sha kenan ta zamto tauraruwa a idanun Hamma Yusuf(Miwasmiti)...Tabbas Mahmud ya zamto zautacce kuma makaho akan sauyayyar Bazawara wato khadijarsa duk da kuwa gashi da budurwa(Namiji Baya Kaɗan) ko kinsan hakan nada alaƙa da amfani da sahihan maganin da kuma shu'uman humran Aysha Aliyu Garkuwa??.Nasan ba zaka ku manta da irin kima da kuma darajar da Aysha ke dashi acikin Idanun Sheik Jabeer ɗin ta duk da kuwa shekaru sunja anma jinta yake tamkar budurwa 'yar sha bakwai duba littafin (Garkuwa) sirrin hakan na tare da Ingantattun kuma sahihan magungunan Aysha Aliyu Garkuwa Wato Garkuwar Marubuta da kuma Ma'aurata na tabbata kunsan da cewa basirarta ba'a iya rubutun littafi ya tsaya ba hadda inganta rayuwar ma'aurata ta hanyar kawo musu Nagartattun abubuwa Ga duk wacce ta shirya saya seta tuntuɓi number ta 09097853276 muna iya tura kayan mu aduk inda kuke afaɗin Nigeria harma da ƙetare Dan Allah 'yar uwa idan baki shirya siyaba kada kiyi min magana muɓatawa kanmu lokaci ga kuma account no 0005388578 Jaiz bank AISHA ALIYU GARKUWA, kina iya tura kuɗinki kafin ma ke min mgn duk abinda na irga akwaisu Available...._ 🤝🏻🤝🏻🤝🏻🤝🏻🥰😘sai.kunzo. sayan na gari maida kuɗi gida, By *GARKUWAR MARUBUTA* [19/07, 7:44 PM] Halimatu A/rahman Sadeeya: 📝🍇✨💫⏰🤴🏻👹❤️❤️❤️🍇 *SAKAYYAH* Page 2 NA *AYSHA ALIYU GARKUWA* 🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 *FREE PAGE* *LITTAFIN SAKAYYAH NA KUDINE, WANNAN FREE PAGE NE, ƳAR UWA KI BIYA KI KARANTA CIKIB AMINCI BA HAƘƘIN WANI GABA GAREKI 1k ne kacal kuɗin littafin duk da yawa shi. 0661110170 GTBank AISHA ALIYU GARKUWA, ta nan zaku biya, sai ki turo min shaidar biyanki ta WHATSAPP 09097853276. In kuma baki da account ko matsalar Network ZAKI IYA SAYAN KATIN MTN sai ki copy number's ɗin katin ki turo min ta WHATSAPP. 09097853276. Kada ki kirani in kin san ba kayan Ɗa'a kike soba. In dai littafine kiyi min mgn a whatsapp ɗin.* *WOHOHO IN KAJI ANA ƘI GUDU TABBAS SA GUDU NE BEZO BA* _Ina kuke Ma'aurata masu sha'awar ganin sun zama taurari kuma fitilu a idanun da zuƙatan mazajensu Uwar gida,Amarya,Tsakar gida, kai har ma da tan kaɗen gida Shararru kuma ƙasaitattun magungunan matan dans saba kawo muku nau'ikan sirrin sahihan magungunan ma'aurata daga hannun. *AYSHA ALIYU GARKUWA* Garkuwar Ma'aurats ayau ma na dawo muku da Ingantattun magungunan mata masu kyau da inganci domin gyara kanki, ko ƙanwarki, ko ƴarki, ko a miniyarli, damake kanki ki zamto tauraruwa a idanun mijinki...Muna da Ingantattun Abubuwa kamar haka_ :_Munada Garin mallaka, garin maɗi, garin Hakkin mayi, garin ɓelɗamhi Garin ilanwaddihi, Dukansu ƙananan robobin akan dubu uku uku ne kacal Gumbar da ba'a baiwa mai kishiya, koriyar gumba, gumbar madara, Gumbar kolli mai kellin al'khairi, Gumbar Riɗi wato 3 in 1, Gumbar makwaranyi, dukansu a kan dubu uku uku ne ƙananan robobin, sai ta kwalli da ridi da Uku al'khairi da 3 in 1 su dubu biyar biyar ne. Masin Maliƙi mai masifar ƙarfi da matse mace, ta dawo da sabon budurci shi ƴar mitsilar robar 7k ne kana ga masin Daɗi har Maɗigan 5k ne kacal Akwai, kwanon ƙasaitacciyar mace mai masifar kyau da ratsa jiki da samar da inƙantacciyar ni'ima yanada abubuwa masu kyau haɗinsa, 8k ne Zumar goron tula mai masifar kyau, tsumin dabino, mai ratsa jiki, tsumin Riɗi mai ƙarfi, Furar Mata mai tsastsafo da ni'imantaccen damshi, su duka dubu uku uku ne, haɗin Cida kaza, kala biyu ne akwai na 18k shi yanada su tsumi da kwai da rubutu, sai kuma ɗaya haɗin shi 13k ne Ciccibi Abodi, shi 19k ne Tsumin Ɓaure, tuwon ɓauren, duk 3k ne kana akwai maganin sanyi sadidan, wanda bani da haufi a kansu set ɗin 10k ne, rabinshi kuma 5k. Ko mai ciki zata shashi baida matsala, infection ko na cikin mahaifane yana magninsa da uzin Allah. Sai su butar sirri, audugar babbar mace, da dai sauransu... Sai kuma fannin ƙamshi kasance da Shu'umin ƙamshi wanda ze gigita ƙwaƙwalwar Oga tare da jin ko wacce mace bata kaiba...._ _Shin ko kina da labarin Miskilinci da ƙasaitar Rayyan Naaan amma lokaci ɗaya ya zamto zautacce sakali akan soyayyar Jannart bakomai Jannart ta riƙe ba face sirrinkan gyara da kuma shu'uman humran da kulaccar sirri na Aysha Aliyu Garkuwa(Tubali) tabbas taga tasirin haka domin Naanunta ya zame mata tamkar bawa_ _Shin ko kinsan sihirtaccen haɗin da Aysha ke sha kenan ta zamto tauraruwa a idanun Hamma Yusuf(Miwasmiti)...Tabbas Mahmud ya zamto zautacce kuma makaho akan sauyayyar Bazawara wato khadijarsa duk da kuwa gashi da budurwa(Namiji Baya Kaɗan) ko kinsan hakan nada alaƙa da amfani da sahihan maganin da kuma shu'uman humran Aysha Aliyu Garkuwa??.Nasan ba zaka ku manta da irin kima da kuma darajar da Aysha ke dashi acikin Idanun Sheik Jabeer ɗin ta duk da kuwa shekaru sunja anma jinta yake tamkar budurwa 'yar sha bakwai(Garkuwa) sirrin hakan na tare da Ingantattun kuma sahihan magungunan Aysha Aliyu Garkuwa Wato Garkuwar Marubuta da kuma Ma'aurata na tabbata kunsan da cewa basirarta ba'a iya rubutun littafi ya tsaya ba hadda inganta rayuwar ma'aurata ta hanyar kawo musu Nagartattun abubuwa Ga duk wacce ta shirya saya seta tuntuɓi number ta 09097853276. muna iya tura kayan mu aduk inda kuke afaɗin Nigeria harma da ƙetare Dan Allah 'yar uwa idan baki shirya siyaba kada kiyi min magana muɓatawa kanmu lokaci idan kuna ga account no da zaku tura kuɗinku ta ciki masu son kayan Ɗa'an 0005388578 Jaiz bank AISHA ALIYU GARKUWA sai ki turo min shaidar biyanki ta WHATSAPP 09097853276...._ 🤝🏻🤝🏻🤝🏻🤝🏻🥰😘sai.kunzo. sayan na gari maida kuɗi gida, Cikin fesa sassayyan numfashi, Modibbo ya ci gaba da faɗin. “Kuji falalar Allahu rabbil samawati garemu, ubangiji yana sonmu yana tausayin mu, yana kuma jinkanmu." Ya dire mgnar yana ɗan sauƙe wani numfashi dan Allah ya sani ya fara jin bakinshi ya gaji da mgna. Cikin tattausan muryarsa yaci gaba da cewa. Daga Abdullahi ibn Busr, Allah ya yarda dashi, yace: (Ya ma'akin Allah! Shari'o'in Musulunci sunyi yawa a gareni, saboda haka ka nuna mini wani abu da zanyi riƙon da shi. Sai Manzon Allah (S.A.W) yace masa. (Kar harshenka ya gushe yana ɗanye daga ambaton Allah. Kuma mai tsira da amincin Allah yace: (Wanda ya karanta harafi ɗaya daga littafin Allah yana da ladan kekkyawan aiki ɗaya, shi kuma kekkyawan aiki ɗaya yana da ladan misalin goma. Ba ina nufin Alif lam Mim harafi bane, A'a. Alif harafi ne, Lam harafi ne, kana shima Mim harafi ne.”. Wani irin mayataccen kallo Samira ke bin lips ɗin Moddibo dashi, tana mai kallon dukkan yadda yake motsasu, da yadda tattausan sajensa ke zuba ƙyalli ƙawarta Ikilima Ibrahim ce ta ɗan taɓata da kafa alamun wannan wanne irin kallo ne. Yayinda gefen damansu kuwa, wata madaidaciyar macece, Hadiza Muhammad Yahaya, wacce take cikin sabbin dalibai. Kallon da Samira Sani keyiwa Moddibo ne ke bata mamaki. Shi kuwa Moddibo a hankali yaci gaba da cewa. Kuma daga Ukbatu Ibn Amir Allah ya yarda dashi yace: Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi. Ya fito alhalin muna cikin rumfa sai yace: (Wannene daga cikinku zai so ya fita kullum da safe zuwa ƙoramar Buɗhan ko Aƙiƙ ya dawo da taguwa biyu masu manyan tozuna ba tare da yayi wani laifi ba ko yanke zumunta ba? Mukace masa muna son haka. Yace: (Ɗayanku yaje Masallaci ya nemi sani, ko ko ya karanta ayoyi biyu daga cikin littafin Allah, mabuwayi mai ɗaukana, yafi masa taguwa uku ayoyi huɗu sun fi masa taguwa huɗu da kwatankwacin adadinsu na raƙuma.) Kunga ashe muna ɓarar da damarmakinmu riƙe da waya ba tare da mun samu mun ribaci ilimin da iyayenmu da malanmu suka bamu ba. Kuma mai tsira da Amincin Allah yace: (Wanda ya zauna a wani waje, bai ambaci Allah a wajenba, wannan zai zamanto masa abin bibiya a wajen Allah, wanda ya kwanta a makwanci bai ambaci Allah a wajenba shima zai zamanto masa abin bibiya a wajen ALLAH. Kuma mai tsira da amincin Allah yace: (Babu wasu mutane da zasu zauna a majalisi da basu ambaci Allah a cikinsa ba, kuma basu yi salati ga annabinsu ba, face ya zamo musu abin bibiya, in Allah yaso yayi musu azaba, in yaso kuma sai ya gafarta musu.” Jujjuya idanunsa yayi fuskarsa cike da shauƙin son Mahaikin Allah Muhammadu Rasulullah, da sahabbansa, Wani irin sassayan numfashi ya fesar tare da lumshe idanunsa, wanda yakan shiga wannan yanayi a duk lokacin da yakeyiwa ɗalibansa nuni da al'khairan dake cikin ammaton Allah da bin sunnar manzonmu abinkoyinmu abinsonmu da sahabbansa masu daraja. Ita kuwa Khausar ƙasa tai da idanunta. Sai kuma ta ɗan ɗago ta kalleshi jin tattausar muryarsa yaci gaba da cewa. “Kuma mai tsira da amincin Allah yace: Babu wasu mutane da zasu tashi daga wani majalisi da basu ambaci Allah a cikinsa ba, face sun zama kamar sun tashi daga kan *mushen jaki ne* kuma zai zamanto musu abin dana sani)”.... Ya ƙare mgnar da haɗe kan yatsunsa duka, kana sai ya buɗasu a tare da ware tafin hannunsa kamar ya sake abu, alamun ya dasa babbab ɗamba, ya gama da wannan yankin. Gaba ɗaya hankalinsu tunaninsu duk yana kansa, domin suna matuƙar jin dadin yadda wasu lokutan idan ya shiga aji yake tunasar dasu mahimman abubuwan da suka cancanci musulmi ya lizamcesu. Yayinda wasu kuwa da sam baya shiga ajujuwansu cike da son salon sa suke sauraronsa, kasan cewar makarantar nada yalwar malamai kuma shi aiyuka sun mai yawa shisa ba dukkan class da suke dashi yake shigaba. Shi kuwa Moddibo cikin alamun gajiya da yawan motsa lips nasa da yayi yaci gaba da cewa a gaggauce. “Mu farka mu ribaci wannan shekarar dukanta kada muce dan wannan wata na Ramadan daya shuɗe, zamu bar wasu ayyukan ibada, mu jure mu zamo dasu ɗabi'armu a kullum domin shi ubangiji ka gafartawa bayinsa, a duk sanda yaso ya ainta wasu daga azaba zuwa rahmarsa madaumiya, mu wasar da wayoyin nan mu ruggumi Alqur'ani mai girma da tasbihai ya zama dai ita wayar nan sai time to time zamu riƙe ya ke mai karatu dake nake." Ya faɗi hakan yana nuna gefensu Samira dake buɗe da littafi a gabansu. Sai kuma ya ɗan gyara saƙale Lapel Microphone din a wuyar jallabiyar jikinsa dan yaji muryarsa tana ƙasa sosai alum yadan zame kaɗan, da ɗan sauri yace. “Zaku iya duba Muslim (1/554) Abu Dawud (4/264) da waninsa duba Sahihul Jam'i, (5/342). Tirmizi duba Sahihul Tirmizi (3/140) Abu Dawud (4/264) da Ahmad (2/389) duba Sahihul Jami (5/176) Allah shine mafi sani... Abinda nace dai-dai Allah ya haɗamu a mizanin ladan abinda nai kuskure Allah ya gafartamin.” Ya rufe mgnar da addu'a tare da juyawa ya fita. Sukuwa gaba ɗaya numfashi suka sassauƙe, yana fitowa Malam Jamil na isowa wurin, dan shi zai shiga ya shaida musu kwanakin da aka ƙara. Kai Modibbo ya kauda gefe, jin Aminin nashi na cewa. “Fattanah maza yi gudu ki shiga aji kada in rigagi, shiga, dan in na rigaki nima yau gadin aji zansa kiyi mana”. Da sauri Khausar din ta juyo tare da kallon shi cikin alamun yanai musu barkwanci tace. “Malam ko ta window ma zan shiga”. Murmushin yayi tare da cewa. “Har yanzu baki girmi shiga ta window ba FATTANAH”. Da sauri tace. “Toh ai banyi jikiba, ka gani”. Kawai sai ta kama jikin window alamun zata zauna ta wajen sai ta juya ta ciki. Cikin yamutsa fuska Moddibo yace. “Ke bar nan,”. Ai da sauri ta diro tare, da nufar ƙofa, tana tura baki. Shi kuwa Malam Jamil cikin tsananin son yarinyar sabida ƙwazonta da jan da kwanyarta keyi kana da ƙawancenta da ƙanwarsa Asma'u Ahmad ya bita da ido. Rungume Moddibo yayi tare da yin mgn murya can ƙasa. “Tuba mukeyi Moddibo ai mana tsawan a hankali ka mance baka cire Lapel Microphone ɗinba, har nima tsawar ta razanani”. Wani irin nannauyan numfashin Moddibo ya sauƙe tare lumshe idanunsa. Shi kuwa M Jamil murmushin yayi kana kuma ya sake shi yace. “Lokaci na tafiya sai na fito na sallami maza kam”. Kai Moddibo ya gyaɗa tare da sauƙa ƙasa. Goma dai-dai aka tashi islamiyan gaba ɗaya duk ɗaliban suka koma gida bayan M Jamil ya musu bayanin dalilin ƙarin hutun, wanda kuma suma sunga hakan. Ƙarfe ɗaya dai-dai suka tashi daga taron tattaunawa da malaman nasu baki ɗaya. Bayan sunyi sallan azahar ne, kana duk suka tafi, ma'aikata sukaci gaba da aikinsu. A gidansu Khausar kuwa. Khausar ce kwance bisa 3 str daga ita sai yar doguwar rigar material mai taushi a jikinta, Pink collor, sai hular sanyi data sa a kanta, yayinda himilin gashinta yayi tub-tub a ciki. Da alamun bacci take sonyi. Cikin sanyi ta buɗe ido ta tare da juyowa ta kalli Momynta dake fitowa daga kitchen ɗinta, hannunta riƙe da plate da yankakkun fruits a ciki masu sanyi, gefen ta ta zauna bisa 1 str ta ɗaura plate ɗin kan cinyarta tare kallon Khausar ɗin data miƙa mata hannu alamun ta bata. “Tashi kije ki ɗebo Uniform ɗin ku, nasan yanzu ya bushe kizo ki goge muku kafin a kira magriba”. Numfashi mai ɗan sanyi Khausar ɗin ta fesar tare da miƙewa zaune, ita kuwa Momy tafin sawun ɗiyar Tata take kallo cike da ganin kamannin sawunta dana ahlinta. Hannu tasa ta ɗauki inabi guda uku. Kana ta miƙe tsaye tare da juyawa ta fita. Ita kuwa Momy da idanu ta rakata. Tana fita a barandar ta tsaya tare da ɗan sa hannunta na dama ta riƙe ƙugunta. Amina ce ta fito daga side din Gimbiya Bunayya, mahaifiyarsu kenan, uwar gidan Lamido, Wacce daga itana sai Maman su Khausar wacce itace amaryarsa. Wani irin kallo Amina tayiwa Khausar tare da cewa. “Hamshaƙiya, cin abu a tsaye ba koyarwar musulunci bane”. Fuska Khausar ɗin ta ɗan yamutsa tare da cewa. “Ngd”. Sai kuma ta miƙawa Aminu ƙanin Amina wanda yake gefenta. Da sauri Amina ta kwaɓe hannun yaron da bazai gaza shekara goma sha ɗaya ba tare da cewa. “Makwaɗaicin baza, in zakaci akwai a fridge kaje a baka”. Ido Khausar ɗin ta zuba mata, sai kuma ta sauƙe numfashi dan batayi mmkin hakanba, cikin alamun kasalan da baccin da takeji ya sakar mata, ta nufi wurin shanyan nasu, a hankali take tafiya, dan ganin shanyan nasu yana can har bayan Part ɗin Hajia Bunayya Umma. “Wannan daga gani ma aikin Ramadan ne, shine zai zo yayi mana shanya har nan, zaice waɗan can igiyoyin tsawonsa bazai kaiba”. Ta ƙare mgnar tana nufar can. A hankali ta fara janye shanyan, har ta isa dai-dai window Hajia Bunayya, cikin mamaki ta ɗan tsaya jin yadda Umman ke mgn da faɗa-faɗa. “Kada in damufa kake cewa. Kasan kuwa irin tashin hankali da nake ciki duk sanda na buɗi idanuna na kalli Haiydar a matsayin ɗan Lamido Yariman Gembila kuwa, ko ka mance shine ɗan sa na miji babba, shin baka ganin iyakata da mulki sai dai gani sai hange tunda shine ɗa babba akan Aminu na. Kai bakaga yadda komai zai juye min ba a gaba, ina gani sarauta zata koma ɗakin Aysha ƴaƴanta ne zasu mulki masarautarmun”. Sai kuma tayi shiru alamun tana sauraron abin da ake cewa a ɗaya sashin. Ita kuwa Khausar cike da tsoron halin irin na Umma, gashi dai abinda taji, amman koda zata kwana gayawa mahaifiyarsu bazata taɓa yardaba, domin Umma bata taɓa nuna kishinta a kanta, shiyasa ta ɗauki dukkan yarda ta bata. Cikin tsananin tsoro Khausar ɗin ta zaro ido ta tare dasa tafin hannunta ta dafe ƙahon zuciyarta, jin Hajia Bunayya na cewa. “Wallahi tallahi billahil azeem zanyi komai dan ganin bayan Aysha da yaranta, zanyi duk abinda ya kama domin in kauda Haiydar a matsayin yarima mai jiran gado, dan wlh Allah zan iya kasheshi kowama ya huta!...”. Cikin tsananin kaɗuwa Khausar ta juya da sassarfa ta koma sade ɗin Maminta, tana isa kawai sai ta watsar da kayan bisa kujera. Da sauri ta kamo hannun mahaifiyar tata tare da cewa. “Momy! Momy dan Allah ki biyoni zo kiji wani abu”. Ta ƙare mgnar a matuƙar kiɗime, wanda hakan yasa dole Hajia Aysha ta bita a baya. Ita kuwa da sauri take jenta, har zuwa bayan window Hajia Bunayya. Cirko-cirko suka tsaya, Ita kam Khausar cike da firfito da ido waje take sauraron abinda Hajia Bunayya ke faɗi. Momy kuwa wani irin...! A hankali M Jamil yayi parking a bakin gate ɗin gidansu Moddibo juyowa yayi ya kalli Moddibo dake gefensa yana lallatsa system nasa. “Toh wazai fita ya buɗe mana gate ne kam?”. Ba tare da ya ɗago ya kalleshiba ya ɗaga kafaɗarsa ɗaya tare buɗe tafin hannunsa alamun Oho. Kai M Jamil ya jujjuya tare da cewa, “To bari ni buɗe”. Kai ya kuma gyaɗa masa alamun. “Toh”. Murmushin M Jamil yayi tare da fita ya buɗe gate ɗin, kana ya dawo yaja motar suka shiga ciki. Parking yayi kana suka fito suka nufi cikin gidan, Kai tsaye sashin Innayin suka wuce. Wani irin yalwataccen murmushin M Jamil yayi tare dayin saurin ya haura kan barandar zama yayi daɓas bisa tattausan carpert ɗin dake shimfiɗe a barandar. Innayi na kwance yayinda Ummin Jamil kuwa ke gefenta tana ɓare mata banana. Itama yalwataccen murmushin tayi tare da miƙawa Moddibo ayaban data ɓaren. Amsa yayi tare da juyowa ya ɗan kalli M Jamil da ya zame ya kwanta bisa carpet ɗin tare da ɗaura kansa bisa cinyarta, cike da so, ƙauna, shaƙuwa, tausayawa, yace. “Ummina kin san irin farin cikin da nakeji a raina kuwa in na ganki?”. Murmushin kawai tayi dan ita bazata iya cewa komaiba a gaban Innayi sabida Jamil shine ɗan ta na fari, kuma su nan Gembila sashine na cikakkun Fulani. Kawai dai abinda ta sani a baɗini tasan ta fishi farin ciki. Shi kuwa Moddibo gefen Innayi dake kwance da alamun har yanzu nitsuwarta bai ida dawowa jikintaba, hannunta ya riƙe tare da kallon M Jamil. “Kai dan Allah ɗagata kada ka karya mana cinyarta da katon kankan nan”. Ya ƙare mgnar yana gutsuran banana. Shi kuwa Jamil da sauri ya tashi zaune jin Umminshi na ture kanshi tana cewa. “Ai kam gskyarka Moddibo”. Tashin nasa ne, yasa ta miƙe ta nufi kitchen, trayn data shirya kulolin abincinsu ta kawo musu. Ta ajiye a tsakiyar su, Shi kuwa Modibbo a hankali ya kamo hannun Innayin tare da tallabota alamun so yake ya ganta a zaune. Sai kuma duk suka kalli Innayi data buɗe kwayar idanunta jin yana tallabota. Zaunar da ita yayi cikin kulawa yace. “Yanzu me yake miki ciwo?”. Cikin sanyi tace. “Nima kaina ban saniba, kawai dai zuciyata ke a tsinke tsoro nakeji Moddibo”. Da sauri Jamil yace. “Toh Innayi tsoron me kuma kikeji?”. Cikin sanyi tace. “Tsoron kada mutuwa tai mini zuwan ba zata”. Wani irin masifeffen tsinkewan zuciya ne ya riski Moddibo jin Jamil ya ɗan yi yar dariya tare da cewa. “Kada ki damu Innayi ki dena jin tsoron mutuwa, domin ita wajibinmu ne ita. Kuma tsufa ba shine hanyar mutuwaba, ba abin mamaki bane ki rayu ni nan Jamilu in mutu in barki, in bar Ummina da rashina, in bar Aminina Moddibo da rashin Aboki kamata, tabbas a al'amarin ubangiji zan mutu in barku a raye da kuma ƙunar rashina”. Da sauri Moddibo yace. “Yah Salam wai kai J meyasa ne wasu lokutan kalamanka a baibaisuke? Dan Allah kasan abinda zakana cewa”. Murmushin mai sauti Jamil yayi tare da cewa. “Zanfa mutu kam, dole zan mutu to kai dama a gani kake a haka zamu tabbata ne?”. Da hannu Moddibo ya nuna masa Umminsa da haka kawai taji wasu irin zafafan hawaye sun zubo mata. Da sauri Jamil yasa tafin hannunsa ya sharce mata hawayen tare da cewa. “Kada kiyimin kuka kodama na mutu kada ki damu Ummina kinga aminina Aliyu ko to shi zai zame miki madadina”. Da sauri tayi mishi dakuwa. Sai kuma yayi dariya mai sauti tare dace. “Oh su Ummi ana son ɗan fari wato irin bakya son Jamilunki ya mutun nan ko”. Ya ƙare mgnar cikin tsigar wasa kamar dai kakarsa ce, Hakanne yasasu yin murmushin ganin zata kai mishi duka ya ɗan zille yana cewa. “Haka kawai wai kunya wai ni ɗan fari bazakice kina sonaba, toh ni kam ina sonki ina sonki ina sonki Ummina”. Ƙeyarsa ta ɗan buge, kana ta tura musu plate ɗin dake cike da fruits sai kuma ta mimmiƙa musu fork, Innayi kuma yar wannan hirar da sukayi yasa ta ɗan sake kaɗan, duk da har yanzu in ta rufe idanunta tana ganin abinda Allah ya nuna mata daren jiya. Jamil ne ya kalli Innayin tare da cewa. “Dr Jamila tazo ta dubaki ko, dan da safe kafin mu wuce makaranta na kirata tazo”. Kai Ummi ta gyaɗa alamun eh tazo. Frutis ɗin kawai suka ci kana suka miƙe suka nufu part ɗin Moddibo. Suna shiga falon, Cikin sanyi Jamil ya zauna bisa kujera tare da riƙo yatsar Moddibo manuniya, cikin wata iriyar sassayar muryar yace. “Moddibo kasan ina jin farin ciki na musamman in naga Ummina ko?”. Sunkuyar da kai Moddibo yayi tare da zuwa aminin nasa idanu cikin sanyi yace. “J nasani! Na sani dan farin cikin baya ɓuya a fuskarka”. Cikin Muryar da tafi ta ɗazu rauni ido na ciko da hawaye yace. “Amman kuma fa farin cikina raggene, duk daɗin da nakeji in na tuna cewa Ummina ba a gidan Dadyna takeba, inajin ciwo mai yawa a raina, inajin takaicin Kasan cewar mahaifiyata bata gidan mahaifina tana can a wani gidan. Bayan ita tasha wahalar zama dashi cikin talauci, saida yayi kuɗi dai-dai sanda zataji dadin rayuwa ya saketa, gashi yan uwanta ba masu haliba, mijin da Allah ya ƙaddara ta aura shima rayuwar ba daɗi sabida baida ƙarfi”. A hankali Moddibo ya zauna kusa dashi cikin ƙarfafa mishi guiwa yace. “J wanne dadine na kuɗi ya rage wanda bakayiwa Ummi ka tunafa, duk abinda kace kanaso Daddy yana baka, duk kuɗin da zaka nema zai baka, a haka har Makka ka kai Ummi yaranta ka sasu a makaranta mai kyau sanadin su kaƙi kayi aiki a ko ina kace zakayi karantarwa a makarantarsu dan ka tayata basu tarbiyya. Kana kuma yi tunda gashi yanzu sun kusa gamawa, tunda ko Asma'u nanda shekara uku dai zasu gama, secondary School, kace kuma suna gamawa zaka aurar da Asma'u kana ka ɗauki nauyin karatunta, ta na gaba tana gidan mijinta, shi kuwa Bashir na mijine kuma kace in ya gama so kake ya samu jami'atul Madina, in ya tafi can sannan kayi aure kace kuma kana aure zaka ɗauke Ummi da ita da mijinta Malam Ahmad zaka riƙe su, Jamil to meya rage na jin daɗi da baka samawa Ummi ba, ka gyara mata gidan da take, ka gyara mata ɗakinta”. Wani murmushin mai sanyi yayi tare da cewa. “To wai Moddibo da kake cewa haka, rainafa mallakin ubangijine a duk sanda yaga dama zai ɗaukeni daga wannan duniyar, ko ban gama cikace burukana ba, in babuni a raye wa zai maiye musu gurbina?”. Cikin tsuke fuska Moddibo yace. “To dama wa yake da tabbacin rayuwa, yanzu ni in dai naci zan lizanci irin tunaninka Innayi fa bata da kowa a duniya saini. J ni zaka gayawa mutuwa? Ni Aliyu zaka gayawa mutuwa?”. Sai kuma duk sukayi shiru suka zubawa juna ido. Numfashi mai nauyi Moddibo ya fesar kana a hankali yace. “J ka kalleni mana! In zame maka madubi, gwara kaifa, kasan su Ummi kana ganin ta gafa Daddy”. Da sauri M Jamil ya ri ƙa gyaɗa mishi kai tare da tuno maraicin aminin nasa. Shi bai san iyayensu ba ranar da mahaifisa ya rasu, firgicin abin ne ya tadawa mahaifiyarsa naƙudansa, ta haifeshi kana itama tabi bayansa kamar yadda Innayi ke basu labari. Da sauri M Jamil ya kalleshi jin yana mgn a hankali. “Ba uwa ba uba ba wa ba ƙani ko ƙanwa ba Baffa ba kawu ba goggo ba Yafendo, yanzu ashe bazaka dubi maraicina ba, sai kai ka godewa Allah ba J kaga ni kuwa idan na tuna duk rashin da nayi in naji ƙunci da ciwo sai in tuna. Allah ya azurtani da rayuwa da lafiya kana yayi min ni'imar kasan cewa Musulmi, ya bani hankali ya ƙara min da haddar izu settin, da littattafai masu tarin yawa wanda masu iyaye da dama basu samuba, ya bani sa'a a dukkan karatuna mukayi digire har master's har zuwa P.H.D a makaranta mafi daraja a duniya Jami'atul Madina, kana muka samu gurɓin aiki kuma a can. Wanda ko yau muka koma can da aikinmu a hannu, amman kai ga uzurin daya tsareka, nima kuma da uzurin daya tsareni”. Da sauri M Jamil yace. “Astagfurullah! Astagfurullah!! Astagfurullah!!! Alhamdulillah aboki na gari rahama ne, ai kam ni ga uzurin daya tsareni to amman kaifa Moddibo uzurin menene ya tsareka duk da bana son mu rabu Amman zaso kaje can kayi aikinka da al'bashinka mai daraja”. Kai Moddibo ya kauda tare da cewa. “Uzurina ai a fili yake J Innayi na tana son kulawata”. Da sauri M Jamil yace. “Ba gsky bane Moddibo karo na forko kenan a rayuwarmu daka ɓoye min abinda ke ranka kaƙi ka gaya min me dalilin ka na zama a ƙasar nan bayan saudia na buƙatar ka, kuma harda daman zama da iyalanmu fa muke dashi a can”. Kai ya jujjuya tare da cewa. “J yaushe na zama makaryacin da har mgnata bazata samu karɓuwa a wurinka ba?”. Da sauri M Jamil yace. “No wlh ni mai shaidar ka ne har gaban abadan kai ba makaryaci bane, kawai dai ban gamsu da hujjar bane”. Kanshi ya jujjuya kana ya nufi bedroom ɗinsa, Shi kuwa M Jamil ɗayan ya shiga. A can cikin masarautar Gembila kuwa, Cike da kaɗuwa Khausar ta... Ta juyo ta kalli mahaifiyarta sabida jin kalaman da Hajia Bunayya ke faɗi. “Eh Sulaiman a kawo min mashin ɗin lipan mai kyau wanda zaiyi dai-dai da Haiydar, A kawo fari dan yafi son komai nasa fari”. Sai kuma ta ɗan yi jim, alamun tana sauraran abinda ake faɗi a ɗaya sashi, dariya mai cike da sakewar zuciya tayi tare da cewa. “Ai kaima kasan shi na musamman ne, Yarima ne fa, mai jiran gado, kuma gashi sunan Babanmu gareshi, in banji dashi ba da waye zanji”. Ita kam Khausar cike da mmki take kallon yadda mahaifiyar ke sakin wani murmushi mai cike da yarda da jin daɗin kawaici da ihsanin uwar gidan tata, Yayinda ita kuwa Khausar take kallon abun da idanun basira, tana tuna kalaman da taji ɗazu da wanda Umman keyi a yanzu, a sanyaye tace. “Marching kuma?”. Daga ciki kuwa sai suka tsinkayo muryar Asiya na cewa. “Ehye Haiydar ɗan gatan Umma da Lamido, yaron nan kunaji dashi,”. Murmushin mai cike da manufa tayi tare da kallon inuwar Khausar da Mami ta jikin window nata, cikin ɗan daga sauti tace. “Kema ai ɗan lelenki ne,”. Miƙewa tsaye Asiya tayi tare da cewa. “Yauwa dan Allah Umma ni zanyi masa albishir”. Kai ta gyaɗa tare da cewa. “Amman ba yauba sai marching ɗin ya iso”. Numfashi mai sanyi Momy ta fesar tare da kamo hannun Khausar suka juya suka tafi. Ganin tafiyar sune yasa Hajia Bunayya yin kwaffa tare da cewa. “Uhum zanyi mgnin kine, shegiyar yarinya mai masifar wayon tsiya da sa ido, tama fi mahaifiyar tata wayo da fahimtar manufar mutum”. Su kuwa, suna shiga falon Khausar ta juyo a hankali tace. “Dan Allah Momy kada ku bari Haiydar yaja marching yayi ƙarami dudu du fa shekarunsa sha 13 ne kawai dan yanada saurin girma”. Da sauri ta juyo ta kalli Haiydar da yanzu shigowarsa, kanshi ya nuna da yatsarsa manuniya tare da cewa. “Ni ne ma yaron? To da shekaru nawa kika fini dabino uwar tsufa, ba shekara ɗaya rak kike bani”. Yes tabbas kam shekarunsa 13 ne, amman in ka ganshi zakayi zaton yaje 16, domin yanada girman jiki, kuma irin masu wayo da halin girman nanne shiyasa sam bazaka tantance shekarunsa ba, ya fita jiki da tsawo sosai. Dan in ka gansu zakayi zaton shine babban irin ya bata shekara ukun nannan ne”. Kai ta jujjuya tare da rumtse tafin hannunta, kana cikin sanyi tace. “Dan Allah Momy kada ki bari dan Allah a wannan karon dai ki yarda dani”. Kai Hajia Aysha ta gyaɗa mata tare da cewa. “Zan duba." Cikin kwaɓe fuska Haiydar ya turo baki gaba tare da cewa. “Plesse Momy kada kibi ta kan mgnar ta”. Still kai ta gyaɗa masa shima tare da cewa. “Toh zan duba”. Cirko-cirko sukayi a gabanta. Dan dama da haka take yanke musu taƙaddama. Idanu ta ɗan lumshe jin an kira sallan magrib cikin fesar da sassayan numfashi tace. “Lokacin salla yayi, maza muje muyi salla”. Ba musu duk suka juya, shi Haiydar waje ya fita yana cewa. “Ramadan zomu tafi masallaci”. Ita kuwa Khausar ɗakinsu ta nufa tana cewa. “Raudat zomuje muyi salla." Da sauri kuwa sukabi bayansu. A can gidansu Moddibo kuwa, M Jamil ne, ya kalli dun-duniyar sawun Moddibo lokacin da suka fito kan barandar da alamun al'wala sukayi. A hankali yake taku cikin nitsuwa, yayinda yake motsa laɓɓan bakinsa yana taibihi. Sai kuma ya maida kallonsa kan sumar ƙeyarsa dake kwance lip-lip tayi irin naɗin nan mai kamar taburma. Kusan a tare suka sauƙo, Hango Ummi da Innayi zaune bisa sallayunsu, da kaskon rushi a tsakiyar su ne, ya sasu juyawa suka nufi waje, sabida tafiya masallaci. A hankali Moddibo ya zira tafukan hannunsa cikin aljuhun jallabiyar jikinsa, sabida wani irin masifeffen sanyi dake fesowa, duk da rigunan sanyin da suka ɗaura kan jallabiyoyin bai tsare musu sanyi irin na garin Gembila ba, musamman ma, a lokacin da magrib ta ƙarato, wanda lokacin sanire ke sauƙa. Kasan cewar masallaci babu nisa da gidan ne, yasa suka, tafi da sawu. A hankali M Jamil ya lumshe idanunsa sabida yadda yake jiyo sautin muryar Moddibo can ƙasa yana zikirin tafiya masallaci. Shi kuwa Moddibo cikin yanayin sanyin da yakeji yake motsa laɓɓan sa a hankali cikin dadɗan sauti can ƙasa-ƙasa yake cewa. اللَّهُـمَّ اجْعَـلْ فِي قَلْبِـي نُوراً، وَفِي لِسَـانِي نُوراً، وَفِي سَمْعِي نُوراً، وَفِي بَصَرِيِ نُورًا، وَمِنْ فََوْقِي نُوراً، وَ مِنْ تَحْتِي نُوراً، وَ عَنْ يَمِينِي نُوراَ، وعَنْ شِمَالِي نُوراً، وَمِنْ أَماَمِي نُوراً،,وَمِنْ خَلْفِي نُوراً، وَاجْعَلْ فِي نَفْسِي نُوراً، وأََعْظِمْ لِي نُوراً، وَعَظِِّمْ لِي نُوراً، وَاجْعَلْ لِي نُوراً، واجْعَلْنِي نُوراً، ألَلَّهُمَّ أَعْطِنِي نُوراً، وَاجْعَلْ فِي عَصَبِي نُوراً، وَفِي لَحْمِي نُوراً، وَفِي دَمِي نُوراً، وَفِي شَعْرِي نُوراً، وفِي بَشَرِي نُوراً، أَللَّهُمَّ اجِعَلْ لِي نُوراً فِي قَّبْرِي... وَ نُوراَ فِي عِظاَمِي، وَزِدْنِي نُوراً، وَزِدْنِي نُوراَ، وَزِدْنِي نُوراً، وَهَبْ لِي نُوراً عَلَى نُوراً Dai-dai lokacin da yazo ƙarshen addu'ar suka isa bakin masallacin. Kusan a tare suka haɗa baki wurin yin addu'ar shiga Masallaci. ”أَعوذُ بِاللّهِ العَظِيـمِ، وَبِوَجْهِـهِ الكَرِيـمِ وَسُلْطـَانِه القَدِيـمِ، مِنَ الشَّيْـطَانِ الرَّجِـيمِ، بِسْـمِ اللّهِ وَالصَّلَاةُ وَالسَّلامُ عَلَى رَسُولِ اللّهِ، اَللَّهُـمَّ افْتَـحْ لِي أَبْوَابَ رَحْمَتـِكَ“ Kana a nitse suka shiga cikin masallacin. Shi Moddibo gefen daman sahun forko ya zauna, yayinda shi kuma M Jamil ya nufi wurin kiran salla... Kasan cewar M Jamil ke ladancin masallacin Moddibo kuma limancin... Bayan an idar da sallane, Khausar ta juyo ta kalli Raudat tare, da miƙa mata littafin Dua azkar, amsa tayi kana ta buɗe daga shafin forko ta fara cikin sassayan sautin yarinta. Ita kuwa Khausar Alqur'anin ta, ta ɗauka tare da fara, rero karatun Alqur'ani cikin zazzaƙar muryarta take biya suratul Nisa'i. A haka har aka kira isha sukayi kana, suka fito. A falon suka zauna baki ɗayansu suna cin abinci. Misalin ƙarfe tara da rabi, Ummi ce zaune gefen Innayi da hijabi a hannunta alamun ta gama shirin tafiya. Cikin kulawa da martabawa tace. “Toh Innayi Allah Ubangijin talikai ya baki lfy yasa zakkan jikine, in Sha Allah gobe koda dare zan zo in kuma dubaki da jiki”. Kai ta gyaɗa cike da jin daɗin kulawar Ummin Jamil cikin ƙarfin guiwar da ta ɗan samu tace. “Amin ya rabbil izzati Fatima ngd matuƙa Allah ya raya miki ahlinki yasa suyi miki fiye da abinda kikeyi min”. Cike da jin daɗin addu'ar tace. “Amin ya Allah”. Moddibo kuwa, kai ya tankwara gefe yana kallon kakartasa, sosai ta rame a dare ɗaya da wuni ɗaya. Haka dai sukayi sallama Jamil ya ɗauke ta suka tafi. Har bakin gate Modibbo ya rakasu. Kai ya ɗan juya ya kalli wata motar dake gefen damansa ƙirar BMW irin dai wacca M Jamil yaja sukaje makaranta, sai dai wacce baƙace wannan kuma farace ƙal mai masifar kyau. Murmushin M Jamil yayi sabida ya fahimci kallon da yayiwa motar ma magana ce. kanshi ya juya tare da cewa. “Lafiyarta ƙalau kawai na barta a nanne sabida nan ya dace da ita, tunda ba gida ɗaya mukeba, Allah ya kiyaye wani uzurin zai iya tashi da dare, kaga kamar jiya da kasan Innayi ba lafiya kawai ɗaukarta zakayi ku tafi hospital ko Ummi?”. Ya dire ayar mgnar yana kallon Umminsa da shima Moddibo ita yake kallon. Cikin gamsuwa Ummin tace. “Sosai ma kuwa”. Cikin yin ƙasa da kai Moddibo yace. “Ummi har kema haka zakice, kamar baki san me ake faɗi a cikin gariba, ba cikin gari, bama har cikin gidansu fa, ganin kaskas akemin wasuma ɗaukar abotarmu ta tun yarinta sukeyi a matsayin na maida J saniyar tatsa." Cikin sanyi Ummin tace. “To Moddibo ai shi ɗan adam ba'a biye masa”. Da sauri Jamil yace. “Yauwa Ummi gaya masa dai kam”. Cikin tsare M Jamil din da ido yace. “Motace dai ta hannunka ta ishemu, kuma ga waccar ma, kasan in bawai baka nanba always muna tare”. Da sauri Jamil ya jujjuya mishi kai tare da jan motar ya tafi. Sashin Innayin ya nufa, cike da zurfin nazari. Tv ya kunnamata tashar Sunna, inda aka sa sautin karatun Alqur'ani mai girma. Ido Innayi ta lumshe jin nitsuwa da salama na diro mata, Saida safe yayi mata kana juya ya fita zuwa Part ɗin sa. Washe gari ranar Alhamis ne, yau babu makaranta ko yan haddan bazasu jeba, shiyasa su Khausar suna gida, Bayan sallan la'asar Asma'u Ahmad ta shigo falon Momy cikin sakin fuska tayi sallama. Da sauri Khausar ta fito daga ɗakin Momy tana cewa. “Wa alaikissalam Giɗaɗo". Murmushin Asma'u Ahmad Giɗaɗo tayi, ƙanwar M Jamil kenan da suka haɗa uwa. Cikin sakin fuska tace. “Jauro”. Fuska Khausar ta kwaɓe tare da cewa. “Wai jauro gsky ni an cuceni”. Murmushin sukayi baki ɗaya sabida daƙuwar da Mamy tayi musu. Cikin kunya Asma'u ta ɗan rusuna, tare da cewa. “Barka da yamma Mamy”. “Barka dai Asma'u ya Umminki?”. “Tana lfy tace in gaidaki”. “Masha Allah Ina amsawa”. Da sauri ta miƙe tsaye jin Khausar ta kamo hannunta. Ɗakinta suka nufa, suna shiga suka zauna bisa gado. Raudat dake kwance kan gadon riƙe da wayan Mamy tana game ne ta miƙe da sauri ta faɗa kan Asma'u. Ruggumi yarinyar tayi tare da cewa. “Autan Mamy tsifa ake yi ne”. Kai ta gyaɗa mata tare da cewa. “Eh kuma gashi har yanzu Adda Khausi bata gama minba, tsifanta zafi”. Hararanta kausar ta ɗanyi tare da cewa. “Da Allah tashi daga nan, nawama da yaya nake tsifan, kin samu ma inayi miki”. Ta ƙare mgnar tana fita daga ɗakin. Jim kaɗan ta shigo riƙe da filas da kofuna guda biyu bisa tray da kuma kayan tea, kan bed side drower ta ajiye tiran kana ta haɗa musu tea mai zafi, sabida rage sanyin da suke rayuwa cikinsa, yasa tea ya zame musu tamkar ruwa, madadin in kaje baƙunta a baka abin sha mai ɗan sanyi, sai a tarbeka da zazzafan shayi. “Gidado bar tsifan nan ga tea". Khausar ta faɗa tana zama gefenta tare da miƙa mata, kofin. Amsa tayi tare da kallon Raudat da ta fice da gudu sabida jin Abbansu ya shigo yana kiranta. Riƙe cup ɗin tayi ba tare da tasha ba, Ido Khausar ta ɗan zuba mata kana tace. “Ya dai Giɗaɗo lfy kuwa?". Numfashi mai nauyi Asma'u ta fesar kana cikin sanyi tace. “Kamar zan biya ɗazu ki rakani”. Ajiye cup ɗin hannunta tayi tare da cewa. “Ina?”. Murmushin Asma'u tayi tare da cewa. “Gidan su Moddibo”. Fuska ta kwaɓe tare da cewa. “Allah ya kiyasheni, me zai kaini gidansu wannan mugun, mutumin da duk duniya bana da maƙiyi sama dashi, duk abin da nai laifine, ni zanje gidansu yace na kai musu fitsara ya dakani a banza”. Murmushin Asma'u tayi tare da cewa. “Yoh ai shiyasa ma ban biyaba dan nasan bazaki taɓa yarda kijeba, kuma dai don shine sarkin masifa da mugunta kawai daga zuwa gidansu sai ya kama dukanki”. Baki ta taɓe tare da cewa. “Yoh ai bazanma jeba ma”. Kai Asma'u ta jinjina a ranta tana raya wata rana zatayiwa Khausar tsiya, ta kwasheta ta kaita. Ajiye kofin tea ɗin tayi tare da cewa. “A'a dubiyar mara lfy cefa Innayinsa ce ba". “Can musu”. Ta faɗa tana kwaɓe fuska Murmushin Asma'u tayi tare da cewa. “Toh naji”. Daga nan sukaci gaba da hira. Washe gari ranar jumma'a, misalin ƙarfe biyar dai-dai Khausar da ta shigo cikin gidan riƙe da hannun Raudat da alamun kitso ta kaita. A bakin mashigar gidan nasu tayi kiciɓis da Amina da Samira sani, Sun iso bakin ƙofar a tare, dole sai ɗaya ya kaucewa ɗaya kafin a samu wurin wuce. Wani masiyacin kallo Samira ta cillawa Khausar tare da jan tsaki. Ita kuwa Khausar tsuke fuska tayi cikin rashin shakka ko tsoro ta goga kafaɗarta da na Samira duk da kuwa Samira ta girmeta ainun. Cikin izza Samira tace. “Ke karere ki nitsu kisan da waye kikeyi”. Ba tare da ta cire idanunta cikin nataba tace. “Toh dodon gori”. Cikin fahimtar caguben baƙar mgnar da Khausar ɗin ta yaɓa mata wanda yafi abinda ta gaya mata ciwo, tace. “Ke nifa uwarki zanci”. Wani bauɗeɗɗen harara da dogon tsaki Khausar taja tare da cewa. “Raudat mu tafi, kada mu tsaya muji, kukan tsuntsaye marasa tushe da gurbatacciyar tarbiya”. Daga nan, ta juya tayi gaba. Samira sani kuwa wani irin masifeffen kallo mai cike da tsana take Binta dashi. Cikin takaici tace. “Wallahi na tsani wannan yarinyar sam bana son ganinta, domin ta zame min madakatar nasarata". Kwaffa Amina tayi tare da cewa. “Bar shegiyar yarinya zanyi mgninta”. Cikin tarin tsana Samira tace. “Kune ma kuka bata dama ai, tana agola sai iyayi take muku, an wani dai-dai ta komai naku da nata, wai hatta makarantarku ɗaya da ita, ni wlh da nice ke sai na zuga Umma ta zuga Lamido tasa an cireta a wannan makarantar, shegiyar yarinya mai kama da ƴan ruwa.” Kwaffa Amina tayi tare da cewa. “Bar hegiyar yarinya, zanyi maganinta”. Ita kuwa Khausar a falo suka samu Mamynsu kishingiɗe bisa carpet saƙale da wayarta a kunne, da alamu waya takeyi, ido ta zuba mata jin tana cewa. “Eh Hajja Nana in Sha Allah, zata zo, don dama cikin azumi suna hutu to kuma rashin lfyar ne ya hanata zuwa, amman yau suka koma makaranta, kuma an ƙara musu hutun mako uku guda, sabida gyaran da akeyi a makarantar in Sha Allah zata zo, a satin nan,". Sai kuma ta ɗan yi shiru, na wasu ƴan daƙiƙu, cikin sanyi da girmamawa tace. “Eh gata nan ma”. Tayi mgnar tana miƙawa Khausar wayar, cikin kwaɓe fuska kamar zatayi kuka ta amshi wayar tare da karawa a kunne murya ciki-ciki tace. “Njam ɓanɗu. Ina yini?". Daga can kuwa cikin irin isa da kasaita ta tsofi masu iko Hajia Nana tace. “Lafiyata lau, ki shirya kuna gama jarrabawar jarabar taku ta bokoko a wutan zakizo nan Jauro yaya inada buƙatar ganinki”. Cikin sauri da alamun akwai zaunanniyar tsama a tsakaninsu tace. “Toh ai muna da hadda yanzuma da aka ƙara mana hutun, kuma zamuna zuwa leson”. A faɗace tace. “Leso mato nace leso mato, ita haddar mu nan ɗin ce miki akayi garin kafuraine, kizo liman Sadu zai baki duk ilimin da kikeso in dai na addinine, na kafurcine dai bamu dashi”. Cikin takaici tace. “Nifa ki dena kafurta mana ilimin mu". Cike da mamaki da al'ajabi Hajja Nana tayi wani dogon salati, tare da sanar da Ubangiji wai itace tana mgn ana bata amsa, ita da mgnar ta take tamkar wahayi a cikin rugarsu kasancewarta itace babba. Da sauri ta katse kiran tare dasa wayar a Airplane mode, ta kifeta gefenta sabida kada Mamynta ta gane. Cikin yin rau-rau da ido tace. “Mamy dan Allah kice mata tayi haƙuri sai ran babban sallah zanje muyi kwana biyu kafin a koma makaranta”. Da sauri Momy ta fara jujjuya mata kai tare da cewa. “Ban isaba Khausar ni dai kam bani da bakin yin taƙaddama da umarni Hajja Nana, ki kwana da sanin can zakije kiyi hutun nan, da kika samu ma bakije kinyi azumi a canba, tun tsawon shekaru takebi tana son hakan kuma bai samuba sabida uzurin da ita kanta ke fadarsa na zuwan ta Umara, bana kuma tace, saboda ke, bazata je Umrar ba, saboda tana so kije ki daɗe kisan yan uwanki su sanki.” Cikin jan dogon numfashi tace. “Mamy ni dai kin san ba shiri nakeyi da ita ba, ko zuwa nan tayi a wuni ɗaya sai tayi min masifa da sharri sama da sau biyar”. Cikin haɗe fuska Mamy tace. “Kuma dole kan umarnin ta da izininta mizanin muhallin zamanki yake, ki fara shiri kawai ma in Allah ya kaimu gobe zan gayawa Abbanku, zuwa ranar jumma'a mai zuwa sai ki bisu in sunzo cin kasuwa kije RUGAR JAURO YAYAH tabbas d....! Littafin SAKAYYAH na kuɗine biya ki karanta cikin Salamah yar uwa. By *GARKUWAR MARUBUTA* [19/07, 7:44 PM] Halimatu A/rahman Sadeeya: 📝🍇✨💫⏰🤴🏻👹❤️❤️❤️🍇 *SAKAYYAH* _Page 3_ _NA_ _AYSHA ALIYU GARKUWA_ 🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 *FREE PAGE* *Littafin SAKAYYAH na kuɗine 1k ne kacal ƴar ki biya ki karanta cikin Aminci ba haƙƙin wani a kanki 0661110170 GTBank AISHA ALIYU GARKUWA sai ki turo min shaidar biyanki ta WHATSAPP 09097853276* *GARKUWAR* taku ce dai MA'AURATA, da masu shirin aure, da masu jego, da yan gayu masu son k’amshi kece raini, da gyaran da zaike maimaita muku dararen forkon kuruciya* Ko kunsan Jikinmu na da sinadaran hormones da suke taimakawa dan’adam akan komai musamman lokacin da mace take mu’amalar aure da mijinta. Mafi akasari wannan hormones din ne ke samun matsala ko su yi sanyi koma su daina aiki kwata-kwata shi ne dalilin da zai sa mace tace bata jin sha’awa ko bata san dadin aure ba. Albishirinku ina da kayan da ke taimakawa wannan sinadaran su dawo aiki tukuru don karkato miki da kimarki wajan mai gida sannan su taimakawa wannan sinadaran hormones dinki su dinka secreting din ni’ima wadatacciya da zata taimaka miki ki gamsu mijinki ya gamsu fiye da tunaninki. Note: Kayana ba sa tsinka ruwan ni’ima suna dai taimakawa hormones dinki ne su tsattsafo da ni’imar musamman wacca cutar sanyi ko dattin mahaifa ya dankarar da su ya hana su yin aikinsu yanda ya kamata. Haka zalika idan kina da kyau ki kara da wanka. Zaki iya amfani da magani na na gargajiya wanda zai gyara miki sex hormones din kullum ki kasance cikin humidify wato cikin damshi mai albarka kamar yanda ake son mace. Yana gyara miki mara. Sai kamshi. Hajiyata daure ki fara amfani da turarena ki ji irin salon kamshin sa salo ne da zai daidaita ki da mijinki ya kankaro miki da kimarki a wajansa. Siyan na gari mayar da kudi gida. Ga masu buƙata ga number' wayata wanda nake whatsApp dashi 09097853276 kimin mgn ta whatsApp in har kin tabbatar kin shirya saya mu dai-dai ta, kayana ba ƙanana bane, shiyasa bana harkan karanta, muddin kinsan baki shirya sayaba Please kada kiyi min mgn ki bari sai kin shirya kuɗinki a hannu, ba ina nufin kayana bana talaka bane, no akwai ƙananan set na masu karamin karfi, banson aimin mgn a ɓatamin lokacin aiyukana a shirme baki shiryaba. Shine karantan da bana so. 0005388578 Jaiz bank AISHA GARKUWA ALIYU. In kin shirya ga number ta ga kuma account number ta wanda in mun gama mgn zaki turo kudin ki, kana insa miki kaya a mota, duk jihar da kike kayana zaije gareki, amman fa in kinada dalilin zuwan nasune🤝🏻sayan na gari meda kudi gida. Set ɗina akwai manya akwai ƙananan set akwai kuma na tsakiya, ƙananan set ɗin daga 40k 35k 30k 25k 20k 15k 10k shine ƙara ɗan cukulan haɗiba bana haɗin kasa da 10k sai kuma haɗin kwanon ƙasaitacciyar mace shi 8k set ɗin tsakiyan su da 50k 60k 70k 80k 90k ne manyan kuma daga 100k ne zuwa yadda zaki iya Hajia ta* GARKUWAR MA'AURATA Cikin sanyin jiki Khausar ta miƙe tsaye tare da juyawa a hankali ta bar falon Mommy ta wuce ɗakinsu. Ɗakin mai girmane wanda ke ɗauke da matsakaici gado ƙiran Italian bed sai durowarsa dake gefe wanda ke ɗauke da ƙofa shida, daga kusurwan gabas babban TV plasma ne da DStv sai tattausan canis carpet pinch color dake shimfiɗe Atsakiyar ɗakin wanda shi ke ɗan rage musu masifeffen sayin tayis ɗin, komai na ɗakin pinch colour ne sai ɗan ratsin fari. Cikin jagulewar zuciya ta kwanta bisa gadon tare da lumshe manyan Idanunta dake cike da ruwan hawaye. Allah ya sani sam bata ƙaunar zuwa Jauro Yaya ko kaɗan, ya zame mata dole ta newa kanta mafita. Ɗan gajeren tsaki taja tare da mirginawa ta juya tsakiyar gadon, kana ta lumshe idanunta, da wannan tunani bacci ya ɗauke ta... Cikin nutsuwarsa da kuma sanyinsa kamar koda yaushe yake tuƙa motar, yayin da M Jameel ke gefen hagunsa kamar wanda akace ya dubi madubin dake gefensa se kuma yayi saurin kallon Moddibo dake Driving cike da mamaki yace. “Kai A.J kaga kamar binmu akeyi fa ko?”. Kai Moddibo ya jinjina tare da ɗan yamutsa fuska anitse yace. “Eh binmu akeyi sai munje gidan Ummi zan tsaya”. Cikin sauri M Jameel ya juyo gareshi tare da ɗan ware idonsa yace. “Kama san ana binmu kuma shine ka ƙi tsayawa? Idan kuma wanda zasu cutar da mune fa A.J?”. Kai Moddibo ya girgiza yana mai cigaba da tuƙinsa tare da buɗe lips inshi a sanyaye yace. “Ai nasan wanda ke binmu fa Alhaji Bashir ne”. Da sauri M Jameel yace. “Waye Alh Bashir?”. Ɗan juyow Moddibo yayi tare da ɗan kallonshi kafin yace. “Babban yaron Malam Arɗo ne”. Cikin sauƙe Numfashi M Jameel yace. “Ok to Meyesa ba zaka tsaya ba?”. Ba tare da ya juyo ba yace. “Nasan magana ce mai yawa yazo dashi, koda na tsaya ma, ba zamu gama ba kuma kaga agefen titi muke baya ga hakama na masa signal ya fahimta”. Kai M Jameel ya gyaɗa tare da faɗin. “Ok shikenan”. Daga nan sukaci gaba da tafi. Suna isa ƙofar gidan Ummi M Jameel ya buɗe ƙofa ya fita dai-dai lokacin da Alh Bashir ya ƙara so fuskarsa ɗauke da murmushi ya miƙa wa Alh Bashir hannu sukayi musabaha cikin sakin fuska Alh Bashir yace. “M Jameel Ko?”. Kai M Jameel ya gyaɗa mishi tare da cewa. “Ya gida ya iyalai ya kuma Baba Arɗo?”. Cikkn sakin fuska Alhj Bashi yace. “Duk Suna lafiya”. Murfin motar M Jameel ya buɗewa Alh Bashir tare da cewa. “Bismillah kashiga”, Sannan ya zagaya gefen da moddibo yake wanda har zuwa lokacin bai fito ba yace. "Bari nashiga ciki sai ka shigo”. Kai Moddibo ya gyaɗa cikin yanayin sanyin magarsa yace. “Nima Ina Shigowa yanzu”. “To sai ka shigo”. Ya fadi tare da juyawa ya nufi cikin gida yashiga bakinsa ɗauke da sallama. Ba lefi madedecin gida ne mai kyau daga farkon gidan ze iya ɗaukan motoci biyu se tank na ruwa dake can gefe tsakar gidan shimfiɗe yake da interlock sai babban sashe guda ɗaya cikin gidan zagaye yake da fulawa wi masu kyau wanda keda alaƙa da Moddibo dan duk inda yake da dama sai ya ƙawatasa da fulawowi, sabida suna samishi farin ciki. Tsarin ginin yayi matuƙar kyau duk da cewa ba babba bane amma komai fess dashi haka zalika madedecin falon nasu da befiye girma ba yayi matuƙar kyau falon na ɗauke da manyan setin kujeru kalar ash da baƙi cai Centre table dake tsakiya da kuma ƙaton TV dake maƙale abango daga gabar da TV akwai ƙaton fanka bayan AC dake maƙale da bango daga yamma da TV zagaye yake da wasu flowes masu kyau da ɗaukar hankali sai tattausan carpet mai ɗan kare kyau dake malale a tsakiyar falon... Cike da so kulawa ƙauna irin ta uwa Ummi ta kalli Jameel dake shigowa tare da sakar masa da murmushin da bata san ya subce mata ba, bayan ta amsa sallama. Cike da farin ciki Asma'u ta miƙe tare da gyara wuyan abaya ɗan baby himar dake zage da fuskarta da ɗauke da murmushi cike da jin daɗi ta rungume M Jameel da faɗin. “Oyoyo Yaya Jameel na Ina yini”. Kanta ya shafa cike da son yar uwar tasa yace. “Lafiya lau my blood ya karatu?”. Cikin murmushin ta amsa da. “Alhamdulillah”. kana ta zauna daga ƙasa kusa da ƙafafunsa, Ummu kuwa miƙewa tayi tana ɗan leƙan bayansa. Murmushi M Jameel yayi domin ya fahimci Moddibo take leƙawa ganin basu shigo tare ba. Cikin yanayin fara'arsa yace. “Kai Ummina ki bari mugaisa kafin ki tambayi 'yan biyun nawa??”. Ka ta girgiza tare da cewa. “A'a gwara in tambaya naji, domin shi yace na muku dambun couscous shiya keso kaga kuwa ai bazan ji daɗi ba in ban ganshi ba”. Murmushi M Jameel yayi yana mai jin daɗin yadda mahaifiyarsa ke nunawa amininsa ƙauna tamkar ita ta haifeshi, yana murmushi jin dadi yace. “To yana mota”. Da sauri ta sake dubansa tare da cewa. “To me yakeyi amota da bai shigo ba?”. Ashagwaɓe yace. “To Ummina mu gaisa mana”. Dawowa tayi ta zauna bisa kujera 2 str, shi kuwa M Jameel zamewa ƙasa yayi zauna daɓas bisa carpet kana ya ɗaura kansa acinyarta murya a sanyaye yace. “Ummina daga shigowa ko gaisawa ba muyiba sannan baki samin albarka ba kika tsareni da tambayar Moddibo”. Hannunta ta ɗauka bisa tsakiyar kasan tare da shafa kansa tana mai cewa. “Ubangiji Allah ya Albarkanci rayuwarku! Allah ya dafa muku acikin dukkan lamuranku!! Ubangiji ya tsareku daga sharrin abinƙi tsakanin mutum da aljan!!! Allah ya baku 'ya'ya masu biyayya tamkar yadda kuke mana kaida Amininka”. Cike da tsananin jin dadi da sassayan salama yace. “Ameen thumma Ameen Yah Ummi”. Hannunta ta ɗan janye daga kansa tare da sake tambayar sa. “Ina Moddibo?”. Ƴar dariya mai sauti yayi tare da miƙewa ya zauna akusa da ita kasancewa kujeran 2sitter ne. gyara zamansa yayi yana fuskantar ta yace. “Moddibo zai shigo amma ba yanzu ba”. Da sauri tace. “Meyasa?”. Cikin saurin shima yace. “Bari dai in miki bayani hankalinki ya kwanta. Muna tahowa ne Alh Bashir babban yaron Malam Arɗo ya biyo mu to suna mota suna tattaunawa. Nasan bazai wuce ƙorafi ya kawo akan mahaifinsu ba”. Tsaresa da ido Ummi tayi kana tace. “ƙorafi akan Babansu kuma?”. Kai ya jinjina tare da cewa. "Eh Ummi saboda Malam Arɗo wani irin mutum ne wanda zamuce mai dukiyar lukudi gashi dai Allah ya bashi dukiya na ban mamaki amma babu wanda ya isa yaci wannan kuɗin kamar abin masifa”. Gyara zama Ummin tayi tare da cewa. “Ikon Allah to sabi da me?”. Numfashin M Jameel ya ɗan fesar tare da cewa. “Tun bayan rasuwar mahaifinsa abubuwan suka ƙazanta. Domin baya sauraron shawarar kowa koda kuwa ƙannensa ne domin shine babba acikinsu dan haka babu mai tanƙwarashi. To fa saidai Allah ya ɗaura masa son Moddibo a zuciyarsa duk abinda Moddibo yace ko kuma ya kawo shawara akai to zaiyi koda kuwa ransa baya so. Duk da wani lokaci zakiji yana yiwa Moddibon ma faɗa akan cewa zaisa shi kashe kuɗi amma koda ya gama surutun daga baya zakiga yayi abin da ya fadan.” Gyara zama M Jameel yayu tare daci gaba da cewa. “To fa wannan dalilin ne yasa muddin 'ya'yansa suna buƙatar wani abu saidai su biyo ta hannunsa Moddibo”. Ka saƙe Ummi tayi tana kallon Jameel din kana cikin sanyin murya tace. “To kada fa hakan yasa yayi baƙin jini awajen 'ya'yansa kasan ɗan adam”. Dariya M Jameel yayi kana yace. “Ummi me Moddibo zai buƙata awajen Malam Arɗo me zeyi da dukiyarsu? Mutumin da baiwa yayansa Bama me zai bawa Moddibo wanda baida shi". Kai Ummi ta gyaɗa tare fesar da numfashi a sanyaye tace. “Hakane kam al'amarin Moddibo da Innayi akwai al'ajabi, domin ko nasan baza su taɓa buƙatar wani abu awajensa ba, duk da kuwa anayi musu kallon basu da wani cikekken jigo acikin rayuwarsu. Amma kuma yanda suke tafiyar da rayuwarsu cikin tsari da hikima da wadata yana bani makaki”. Kai M Jameel ya gyaɗa tare da cewa. “Kinga Koda motar da Malam Arɗo ke hawa tsohuwa ce aƙalla zata kai shekaru ashirin da biyar ko ashirin da takwas amma har zuwa yau ya kasa can zawa, anyi-anyi dashi yaƙi duk yanda akayi dashi ya sauya wata yaƙi kuma kullum ciki bashi ciwon kai takeyi. har kyautar Mota ɗansa Alh Bashir ya bashi amma yaƙi amsa domin atunaninsa daga baya zai fanshe kuɗin sa. Ko gidansa da kike gani yanzu ga gini dai yayi mai kyau amma ɗakunan matansa kamar zauren haka suke babu kujeru bare wani abu shi Tv. Yanzu haka kwanan ake gyaran makarantarsa wanda da taimakon Moddibo akeyinsa kuma adalilinsa ne yake biyan Malamai albashi mai tsoka inba haka ba baki ɗaya makarantar ta koɗe sannan babu albashin kirki saboda Moddibo yanzu aka rushe makarantar ake gyarawa yanzu hutun da aka kara ma gani yake kamar za'a yi masa asara shiryasa yace adawo ko ba'a gama gininba to bayan an dawo yanzu dole aka sake komawa hutu saboda ba'a gama gyaranba yanzu ma cewa yayi dole kada a wuce wata ɗaya da ƙyar Moddibo ya lallaɓasa aka tafi hutun kafin adawo angama gini da kuma tsare tsare sa duk ya buwaye mu da cewa Moddibo na sashi kashe kudinsa”. Ajiyar zuciya Ummi ta sauƙe tare da cewa. “Masha Allah shiko wannan wani irin mutum ne?”. Murmushi M Jameel yayi tare da cewa. “Ummi haka 'ya'yansa ke fama dashi, kin san ku fulani”. Murmushi Ummi tayi tare dayi masa daƙuwa. Aɓangaren Moddibo kuwa. Zaune suke da Alh Bashir bayan sun gama gaisawa shiru na wasu daƙiƙu ya wanzu atsakaninsu kafin. Cikin kulawa Moddibo ya ɗan juyo ya kalli Alh Bashir cikin kulawa yace. “Alh ya akayi?”. Numfashin mai nauyi Alh Bashir ya sauƙe kana a hankali yace. “Mitsss Moddibo Agaskiya al'amarin Babanmu yana matuƙar ɗaure mana kai?”. Lumshe idanunsa yayi kafin yace. “Meya faru!?”. Kai ya girgiza cikin yanayin damuwa yace. “Modobbo wallahi Mahaifiyata bata da lafiya, ance sai anfitar da ita waje, gashi duk cikin mu babu wanda yake da halin biya afita da itan. Kasan halin Babanmu kuma, duk iyakar iyawata yaƙi amincewa. Ni kuma bani dashi”. Cikin sanyi Moddibo yace. “Alh baka dashi kuma”. Kwaffa Alh Bashir yayi tare da cewa. “Wallahi Allah Moddibo wasu lokuta idan akace min Alh Bashir ba ƙaramin ɓaci raina yake ba domin bafa mahaifina ne yabiya min Makka ba. Sannan ba nine na biyawa kaina ba dukiyata bace yasa naje ba. Dalilin Surukina naje wato mahaifin Matata fa ya biya min na samu naje duk wani abu da nake buƙata sai dai Inje wajensa wanda kuma hakan da kunya da kuma zubar da girma. amma mahaifina Allah ya hore masa fiye dana surkina amman bazai taimaka manaba ayanzu ga jinyar mahaifiyarmu dole sai anfitar da ita waje an mata dashen ƙoda. shi kansa yana ɓuƙatar canjin mota lokuta da dama yana tafiya Atsakiyar titi zakaga ta lalace, idan shi baya damuwa da zaginsa da akeyi a gari da rayuwarsa to mu muna buƙatarsa ba mason wani abu ya sameshi kuma bama jin dadin habaice-habaicen da akeyi mana. Shiyasa nazo wajen ka. Dan Allah da Manzonsa kayi masa magana ya kai mahaifiyarmu asibiti. Sannan ya canza motarsa bayan wannan akwai kannen mu mata da suka gama secondary akwai buƙatar su tafi jami'a amma yaƙi sasu domin aganinsa za'a cajesa kuɗi masu yawo dan Allah katemaka kayi masa magana akan waɗan nan abuvuwan”. Ya dire ayar mgnar da haɗe tafin hannunsa alamun roƙo da neman al'farma. Moddibo kuwa ajiyar zuciya ya sauƙe tare da buɗe idanunsa dake lumshe kana a hankali yace. "Insha Allah zanyi masa magana, amma ayanzu da ƙyar zai amince domin da mun zauna zance ɗaya yake nanata min wai na sashi kashe kuɗi amakaranta wai zan talautashi”. Murmushi mai ciwo Alh Bashir yayi tare da cewa. “Muma ko agida haka muke shan complain Koda kudin cefene da sauran abubuwa aka tambayesa zaice Ni bani da kudi wannan yaron Moddibo duk yasa na kashe kuɗaɗenna aginin makaranta”. Murmushin gefen baki Moddibo yayi wanda ke ƙara fitar da ainihin kyawunsa cikin sanyi yace. “Uhufm Malam Arɗo kenan. Ba matsala Insha Allah zanyi magana dashi duk yadda mukayi dashi zakaji”. Ya kare mgnar yana shafa tattausan sajensa. Godiya Alh Bashir ya masa sannan su kayi sallama Moddibo yashiga cikin gida. Shi kuma ya juya ya tafi. Tattausan murmushi Ummi tayi ganin Moddibo cikin kulawa tace. “Babana na kaina sannu da zuwa”. Kasancewar sunan mahaifinta garesa. Cike da ladabi ya zauna yana cewa. “Ummi fatan mun same ku lafiya ya yara?”. Da murmushi afuskarta tace. “Duk muna lafiya ya jikin Innayi?”. “Alhamdulillah Ummi jiki kam da sauƙi sosai ma". Ya kare mgnar yana mayar da kallonsa ga Asma'u data fito daga Bedroom da alama muryarsa taji ta fito, har ƙasa ta tsugunna tare da cewa. “Yah Moddibo ina yini”. “Lafiya Asma'u ya karatu da hadda?”. “Alhamdulillah”. Kai Ya jinjina tare da faɗin. “Meyesa yau bakije hadda ba?”. Kanta aƙasa tace. “Yah Moddibo bani da lafiya ne zazzaɓi ke damuna”. Kallonta yayi na daƙiƙu uku, kana yace. “Asmau kadafa ki biyewa wannan mashiririciyar ƙawar taki, ki dena harƙa da ita sam banason alaƙarta dake tsakaninku. Domin yarinyar bata ji kona misƙala zarratin, bana son ganinki tare da ita dan gaba ɗaya sunanta ya zagaye makarantar saboda rashinjinta sam bata da nutsuwar da za'ayi abota da ita.” Ita dai Asma'u kai take jinjina mishi. M Jameel kuwa ido ya zuba mishi yayinda Ummu kuwa ke murmushi. Shi kuwa Moddibo gyara zamansa yayi tare daci gaba da cewa. “Domin shin abota anaso ayi da na gari, bi ma'ana idan za kayi abota kayi da mutum na gari domin kamar dai misalin: meyin abota da me saida turarene koda ba azata masa ƙamshi ba to baza azata masa wari ba, sannan misalin: mai abota dame zuga-zugi koda yana da haske to ba za'ayi masa zaton haske ba". Ɗan kishingiɗan M Jameel yayu tare da lumshe idanunsa. Shi kuwa Moddibo cikin nitsuwa yaci gaba da cewa. “Manzon Allah (S.A.W) ya kwaɗaitar damu da yin abota da mutanen ƙwarai domin abokin ƙwarai yana daga cikin wanda Allah yayi alƙawarin zai sasu acikin inuwar alarshinsa ranar tashin ƙiyama, amma kuma duk abotar da ba'agina sa saboda Allah da manzo ba to ƙarshensa nadama ce sam wannan FATTANAH bata dace da zama abokiya a garekiba”. Itade Asma'u kanta na ƙasa batare data ɗago ba tace. “Toh Yah Moddibo”. M Jameel dake kishin giɗe idanunsa lumshe kuwa a hankali ya miƙe tare da buɗe idanunsa akan Moddibo dake cigaba da yiwa Asma'u nasiyya akan tarabu da Khausar cikin tsareshi da ido yace. “Wai dan Allah A.S meye haka? kana tayiwa Asma'u huɗubar watsar da aminiyarta shin ita Khausar ɗin sheɗan ka ɗauketa ko kuwa dujjal?”. Ɗago kai Moddibo yayi tare da tsuke fuska yana kallon M Jameel yace. “Kusan haka domin sam yarinyar bata da ɗabi'un kirki”. Kai M Jameel ya girgizi kana yace. “Haba Moddibo yarinyar nan tana fahimtar karatu duk wasu abubuwa da ake koyarwa tana ganewa fiye da duk yan ajinka, kawai rawan kai da ƙuruciya ke damunta, da zaran ta mallaki hankalinta zata dena, amma ka zauna kana ƙoƙarin cusa ƙiyayyarta azuciyar Aminiyarta sam hakan ba dai-dai bane yoh ba ita cema ke taimakawa ƙanwar taka da kake zugawarba ita me take ganewa ma tana nan kai kamar na kifi”. Itade Asma'u kanta na ƙasa tana wasa da yatsun hannunta. Wani kallo mai cike da manufofi Moddibo yayiwa M Jameel tare da taɓe baki kana yace. “Ina ruwanka? bansa bakinka ba da Asma'u ƙanwata nake magana” Kana ya juyo ya kalli Asma'u da har zuwa lokacin kanta ke sunkuye yace. “Maganata kika ɗauka zakiyi amfani dashi ko nasa?”. Da sauri tace. “Naka Yah Moddibo”. Murmushi yayi da faɗin. “Ɗayyit Allah ya miki albarka”. Ɗago kai M Jameel yayi dai-dai lokacin Asma'u ta ɗago kanta, ido yakashe mata ita kuma murmushi ta sakar masa. Ummi dake sauraronsu kuwa sai yanzu tace. “Yawwa Moddibo ka cigaba da samun Ido akan yaran nan dan yaran saida sa ido”. Moddibo kuwa ido ya lumshe tare da gyaɗa kai kana yace. “Insha Allah Ummi na lura J da wannan fitinanniyar yarinyar kusan halinsu ɗaya shima kullum fama nake dashi ya nutsu yaƙi nitsuwa”. Wara ido M Jameel yayi tare da cewa. “Nine bani da nutsuwar A.S?”. duk dariya suka sanya banda Moddibo da yayi murmushi. Abinci Ummi ta bawa Asma'u umarnin ta kawo musu fita tayi ba daɗewa ta dawo hannunta ɗauke da warmers ta ajiye musu M Jameel ne ya buɗe murmushi Moddibo ya saki yana kallon yanda dambun yayi kyau sai tashin ƙamshi albasa da kuma ƙamshin man shanu. Ummi da kanta ta zuba musu tare da mimmiƙa musu plate ɗin. Bismillah sukaui kafin suka fara ci suna kammala ci sukayi wa Ummi sallama sannan suka tafi. Washe gari. Tun wuri Khausar ta tashi amma taƙi shiryawa da wuri seda kowa ya gama shiri ya rage saura ita kaɗai, dan Allah ya sani ita ta tsani ta gama shiri ta tsaya jiran wasu. Ahankali take shan comflakes dake hannunta kamar ba jiranta akeyi ba yayin da Raudat ke zaune gefenta, Cikin fushi Amina ta banko labulen ɗakin cikin kumfar baki tace. “Wallahi Khausar zamu tafi in banda raini da samun waje tuntuni muke jiranki amma kin tsaya feleƙe dan kin san in mun tafi mun barki Abba zaiyi faɗa”. Anutse ta ɗago manyan Idanunta dake lumshe ta watsawa Amina wani kallo kafin ta taɓe bakinta kamar zata ce wani abu sai kuma ta fasa ta miƙe ta riƙo hannu Raudat suka fita bayan ta gama shanye Comflakes ɗin. Ajiyar zuciya Amina ta sauƙe cike da takaici tabi bayan Khausar da haramta, duk sanda tazo da niyyan ciwa yarinyar mutunci da zaran sun haɗa ido zata nemi duk wani karsashinta ta rasa koda suka shiga motar Amina bata tanka taba ita da Raudat keta faman surutu har suka isa cikin sa'a Moddibo beshiga ba zamansu ba daɗewa yashigo as usual cikin shigar jallabiya Onion color da yasha guga kansa sanye da hula malam taɓani kaji ruwan hadith yayin da ya naɗe da hirami jikinsa na fitar da ƙamashin daddaɗan tularensa, cike da ladabi suka shiga gaishesa Amsawa yayi kamar ko yaushe a saman laɓɓan sa. Taɓe baki Khausar tayi aranta tace. “Akwi madaran ƙasaita ana mutun kamar sarki”. Batare daya kallesu ba yace. “Su kawo hadda wiƙiƙi da ido Amina tashiga yi kasancewar itace afarko kuma bata iya ba ya dubi Samira sani yace ta karanta hadda still itama bata iyaba kallon Abeeda Sa'idu yayi yace ta karanta wacce ƙawar Samira Sani ce da ƙyar ta karanta aya biyar aciki sumunin da zasu karanta koda yazo kan Khausar cikin nutsuwa da ƙwarewa ta karato sumuni ɗaya na farkon Suratul Taubah. Kanshi ya jinjina tare da juyowa ya kalli Asma'u Ahmad. Cikin yanayin tsoro ta kawo suminin amman yayi mata gyara biyu. Da ɓacin rai Moddibo ya fitar da wanda basu karanta ba ya basu punishment. Khausar kuwa tasa su gaba ta riƙa dariya baƙin ciki ya cika musu zuciya kamar su mutu ahaka Malam Ahmad dake malamin Tajweed ne shima ya zuwa wurin addar. Har yayi ya gama basu dawo ba seda aka tashi kafin aka ƙyalesu akan punishment ɗin... Da dare. Mamy ce tsaye cikin ƙasaitacciyar shiga, tana zuwa wani irin ƙamshin kulaccar sirri da ta saya wurin Aysha Aliyu Garkuwa. Baki ta ɗan taɓe tana kallon yada Khausar ke shishita sabida uban yajin da ta zambadawa indomei wanda yaji nama da. Kai kawai ta jijjiga sannan tayi musu sallama ta wuce turakar mijinta. Tanaci tana kurɓar ruwan sanyi, tana bawa Raudat har suka gama ɗaukar Raudat tayi suka shiga ɗaki kai tsaye toilet suka wuce brush tayi sannan tayiwa Raudat kana suka ɗaura alwala suka fito. Jikin window Khausar ta nufa da niyyan rufewa Idanunta suka sauka akan Haiydar dake ɗauke da Ramadan zasu shiga sashen Hajiya Bunayya, fasa rufe window tayi cikin ɗan ɗaga murya tace. “Haiydar ina zakuje?”. shima cikin ɗaga murya yanda zataji yace. “inda kika aikemu”. Cikin takaici ta rumtse idonta kafin tace. “Wai Haiydar meyesa karai nani ba dama in maka magana, ko in baka umarni saika riƙa bani amsa kai tsaye”. Bakinshi ya taɓe tare sa fadin. “Acikin gida ma saiki riƙa tambayar ina zanje! Me zanyi? Me zanci? fisabilillah ni bani da ikon da zanyi abu da kaina koda Mamy bata Matsamin irin yanda kike min gsky na gaji”. Bai jira jin amsartaba ya wuce yashiga sashen Hajiya Bunayya, Aseeya yayar Amina na ganinsa ta saki murmushi tace. “Umma ga babanki yazo”. Cikin sauri Hajiya Bunayya ta fito hannunta ɗauke da glass cup na madara tana jujjugawa fuskarta da murmushi tace. “Gashi babana madaran shanu ne mai ɗumi”. Amsa yayi yana murmushi saboda yanayin sanyin dake garin yace. “Nagode Umma”. Jujjuya Glass Cup ɗin yayi kafin ya kai bakinsa da faɗin "Bismillahi”. Khausar kuwa jingina bayanta da jikin bango tayi kafin ta ɗaga hannunta sama cikin raunin murya tace. "(Ya wadud³,Ya zul'arshil makin,ya fa'alillima yurid,As'aluka bi izzatil lati la yura,wa mulki kallazi la yuda)ya Allah katsare min ɗan uwana kada Hajiya Bunayya taci galaba wajen cutar dashi”. Kafin ta shafa ta kwanta lamo agado.... A can side din kuma cikin mugun sauri Hajiya Bunayya ta riƙe hannunsa domin bokan daya basu maganin ya tabbatar musu da zaran anyi Bismillah laƙanin maganin ya karye,ta anshi Glass Cup ɗin da faɗin. “Bari mugani kode da zafi ne kada ka ƙone bakinka”. Kai ya girgizi tare da faɗin. “Ba zafi Umma”. miƙa masa ta sake yi amsa yayi ya sake kaiwa bakinsa da faɗin. “Bismillah”, saurin karɓa ta kuma yi tare da cewa. “Mugani kode sugar bai jibane”. Kai ya girgizi yace. “Kin san ba damu da zaƙiba Umma”. yaƙe tayi da faɗin. “bari dai na ƙaro maka sugar”. Ta faɗa tare da shigewa Bedroom duk aƙoƙarinta na ganin ta mantar dashi Bismillah ba jimawa ta fito ta sake miƙa masa tana jujjuyawa aranta tana addu'ar Allah yasa ya manta da Bismillah. Aseeya kuwa ikon Allah kawai take gani wajen mahaifiyarta ita kuwa Amina tasan komai domin ita ta karɓo maganin wurin boka Karƙuzu. Karɓan Glass Cup ɗin yayi yakai bakinsa kana yayi Bismillah yasha kallon Ramadan yayi yace. “Zaka sha?”. Kai Ramadan ya girgiza alamar a'a... Hajiya Bunayya kam ji tayi kamar ta haɗiye zuciya ta mutu ganin maganin data kashe maƙudan kuɗi wajen amsarsu aranta tace. “Shegen yaro mai ta ammalli da addu'a duk uwarsu ta koya musu yin addu'a akan ko wani irin abu afili kuwa murmushi tayi tace. “Babana sugan yayi?”. Kai ya gyaɗa mata sannan ya shanye bayan sun sake taɓa hirane ya mata seda safe ya fice... Washe gari da safe Ummi ta nufi gidansu Moddibo domin duba jikin Innayi bakinta ɗauke da sallama tashiga cikin gidan atsakar gida taci karo da Innayi dake faman gasa nama irin wanda ake yiwa masu jegon. Cikin sakin fuska Innayi ta mata sannu da zuwa, Murmushi Ummi tayi tare da zama ta gaisheta cike da ladabi tare da tambayarta ya jiki kana ta kama mata aikin suka gama. Bayan sun gama ne Moddibo da M Jameel suka dawo zama sukayi tare da gaisawa Ashagwaɓe M Jameel ya dubi Ummi yace. “Ummi bacci nakeji”. bai jira cewarta ba ya zame ya kwanta tare da ɗaura akansa a cinyarta Moddibo kuwa Hararansa yayi yace. “Kaidai ba zaka taɓa girma”. Tura baki M Jameel yayi amma baice komaiba saboda baccin dake cinsa kwanciyarsa ba jimawa bacci ya ɗaukesa ganin lokaci na tafiya yasa Ummi tace. “Moddibo bani filo ka gani”. miƙewa yayi ba daɗewa ya fito hannunsa riƙe da pillow Ummi ta karɓa ta ɗaura kan M Jameel akai sannan ta yiwa innayi Sallama. Moddibo ya tafi mai data bayan sun hau kwalta Moddibo ya dubi Ummi cikin sanyin murya yace. "Dan Allah Ummi ki riƙa yiwa Asma'u faɗa ta daina ƙawance da wannan yarinyar sam bata da nutsuwa zata ɓata Asma'u da halayyarta na rashin nutsuwa yarinya nada naci in ba da gaske mukayi ba bazamu ci nasara ba da na lura ta shiga ranta koda na yiwa Asma'u magana kan tarabu da ita. Kuma naga kamar ba zata yiba anma idan ya zamana mu biyune muke mata faɗa zata ɗauka”. Kai Ummi ta jinjina tare da cewa. “Insha Allahu zan riƙa yi mata”. Ahaka suka isa gida ya ajiyeta sannan ya koma... Washe gari. Ya kama Juma'a misalin ƙarfe uku Khausar na zune kan 2sitter Raudat na gefenta tana yanke mata ƙumba yayin da Mamy ke riƙe da hisnul Muslim tana Azkhar Asma'u tashigo bakinta ɗauke da sallama miƙewa Khausar tayi tare da rungumeta tace. "Oyoyo Ƙawar arziƙi”, Murmushi Asma'u tayi cikin sigar zolaya tace. “Fattanah kina son karya ni ko?”. Saketa Khausar tayi tare da tura ƙaramin bakinta tace. “Kina so mu ɓata ko?”, Murmushi Asma'u tayi tare da tsugunnawa har ƙasa ta gaisheda Momy cikin sakin fuska Momy ta amsa tana tambayarta Umminta ta bata amsa da. “Tana lafiya, Momy tace ma in gaidaki”. Cikin sakin fuska Momy tace. “Ina amsawa”. Ita kuwa Asma'u cikin girmamawa tace. “Ayyah Momy in ba abinda Khausar zatayi miki ta rakani mana Ummi ta aikeni kuma banason zuwa ni kaɗai”. Sanin Asma'u yarinya ce me tarbiya da nutsuwa uwa uba kamun kai yasa Momy amincewa. Kai ta gyada mata tare da cewa. “Toh kada dai ku daɗe ku kuma kula da kanku banda kula maza”. Cikin jin dadi Asma'u tace. “In sha Allah kuwa Momy”. Ita kuwa Khausar murmushi tayi tare da cewa. “To ni baki nemi izinina ba”. Ta ƙare mgnar tana Shiga Bedroom ɗin ta, murmushin Asma'u tayi tare da bin bayanta kana ta langwaɓar da kai tace. “Ayimin afuwa ƙawar arziƙi”. Hira suka ɗan fara taɓa sannan Asma'u ke sanarwa mata zata raka unguwar Teku ta kai saƙo Ummi ta aiko cikin zumuɗi da son fita ta miƙe tare da ɗaukan dogon hijab maroon colour tasa akan riga da wondon dake jikinta ba tare data tambayi inda zata jeba tace su tafi dan kawai tana masifar son unguwar Teku... Aɓangaren Moddibo kuwa bayan ya dawo daga sallar la''asar, Side ɗinsa ya wuce, Ruwa ya watsa tare da sauya kayan jikinsa, wani tattausan riga da wondo nevy blue mai taushi ya zira, tare da fesa turarensa oud jannah mai masifar ƙamshi, System ɗinsa da wayarsa ya ɗauka kana ya fito, a hankali ya lumshe idanunsa jin yadda sassanyar iskar ke ratsa cikin tattausan sumar kansa da yana iya kwana biyu bai cire hulaba. A hankali yake taka steps din yana sauƙowa ƙasa wani irin masifeffen kyau yayi collor kayan jikinsa yayi matuƙar amsarsa farar fatarsa ta ƙara bayyana, yayinda tattausan sajensa yayi lib-lib gwanin burgewa jajayen lips ɗinsa dake cikin zagayen sajensa da kota million ɗinsa sai sheƙi sukeyi, a hankali yake taka tattausan silifas dake sawunsa. ya nufi can gefen yamma inda wasu kyawawan bukoki na zamani da yake wajen hutuwansa, Wurine mai kyau da ban sha'awa a hankali ya zauna bisa ɗaya daga kujerin dake cikin bukkar da tafi sauran ƙawayuwa da flawers. A hankali yake motsa lips ɗinsa alamun yana tasbihi yalwataccen sumar kansa kamar na larabawa na sheƙi da ɗaukar ido idanunsa na lumshe yana motsa bakinsa a hankali. Cikin nutsuwa Asma'u da Khausar suka fito duk da rawan kai irin na Khausar komai nata anitse takeyi cikin nutsuwa suke tafiya yayinda hijabansu yarufe har takalmansu adedeta suka tara tare da sanar dasu inda ze kaisu. Tafiyar Mintuna ashirin da biyar sukayi suka isa aƙofar gidan. A gaban gate ɗin adedeta ya ajiyesu. Asma'u ce agaba tasa hannunta da babu komai ta tura ƙofan gate ɗin yayin da ɗaya hannu ke riƙe da Kula wanda Ummi ta yiwa Innayi dambun naman kaza. Cikin wani irin shauƙi Khausar ke bin ilahirin gidan da kallo ganin yanda flowes da shuke shuken kayan marmari suka zagaye gidan tamkar garden, Da sauri ta juyo da kallonta kan Asma'u tare da cewa. “Wooow masha Allah. Kai Asma'u wannan gidan waye haka? gaskiya yayi kyau sosai”. ta ƙare mgnar tana lumshe idanunta tare da shaƙar sassayan iskar dake haɗe da ƙamshi flawers da kuma turare jikin Moddibo. Kana ta riƙa bin fulawowin tana shafa duk wanda hannunta ya sauƙa akai saita tsinke takai hancinta kana taja dogon numfashi tare da lumshe ido. Shi kuwa Moddibo tun ƙarar buɗe gate ɗin da yayi ya ɗago kansa yana kallon wajen. Cikin mamaki yace “Khausar Usman Lelelwal a gidan nan”. Hannunsa yasa ya tallabe habarsa tare tsuke fuskarsa. Ita kuwa Khausar cike da shauki ta buɗe hannunta tare da jujjuyawa har hijabinta na buɗuwa cikin ɗan ɗaga sauti tace. “Agaski Asma'u gidan nan ya min komai na ciki sun burgeni gawani irin ƙamshi da suke, ji yanda ilahirin gidan ke fitar da wani ni'imantaccen ƙamshi. Gaskiya gidan nan shine aljannar duniya da alamu kuma mutanen ciki maƙurane wajen tsabta ina son komai na gidan nan”. Asma'u Kam dariyar dake cinta take ƙunshewa ta tabbata da Khausar tasan cewa gidansu Moddibo ne babu dalilin dazai kawota sannan ta tabbata yau juma'a ya irin wannan lokacin Moddibo na gida babu inda zeje. Ita kuwa Khausar juyi ta cigaba da yi tare da sauri ta nufi side din Moddibo steps din ta fara tattaunawa tana shafa furannin dake jere a kan. Saida ta hau har tsakiyar barandar kana ta juyo ta fuskanci yama. “Wooww Masha Allah Asma'u zo ki hau ki gani wlh ina hango bakin Teku kinga yadda ruwa da tsuntsaye keyi!". Ita dai Asma'u hannunta tasa ta rufe bakinta tana murmushi. Yayinda tun shigowarsu Moddibo ya zuba musu idanu saidai sam su basu lura dashi ba,da gudu Khausar ta juya ta fara taka steps din tana sauƙa ta nufi sashen da Moddibo ke zaune tana faɗin. “Wowww gaskiya wannan gidan yayi mugun yimin kyau da ace zan rayu a ciki da wanda raina zaiso zan meda mishi gidan tamkar dausayin farin cikin duniya”. Cikin danne dariya Asmau tace. “Khausar zomu tafi mana”. kai Khausar ta girgiza tace. “A'a ki tafi ni wlh saina cire inabin can da Appel kije kawai”. Ahankali Asma'u tace. “Kizo muje mugaida Innayi sai mu gaya mata kafin ki cire”. dan tasan a irin wannan lokacin tabbas Moddibo na nan shiyasa take mgn a hankali wai dan kar ya jisu. Kai Asma'u ta dafe tare da cewa. “Idan masu gidan kuma suka zo suka sameki fa?”. Taɓe baki Khausar tayi tace. “Gida kamar wannan masushi bazasuyi rowa ba, kuma ai nan kamar babu kowa babu wanda zaizo”. ta faɗa tana komawa inda inabi yake tasa hannu ta fara tsinka tana tsalle jin hijabinta zai takurata ne yasa ta zare hijabin tare da ajiyeshi kan kujerar dake ƙasan bishiyar. Middibo kuwa dafe kunci yayi yana ganin ikon Allah Aransa yace. “Yarinya kamar ba mace ba dubi yanda take tsalle kamar biri wannan ba budurciba abinda yafi budurcima zata watsar domin yasan illar hawa bishiya yakan buɗa mace duk da cewa ita ba hawan tayi ba. Tunaninsa ne yakatse asanda ta nufi bishiyar Appel tsalle tayi da niyyar tsinkowa dan bishiyar Appel irin yan masaƙaitan nanne, tsalle ta kuma yi amman ta kasa ga dai hannunta na taɓawa sede baza ta iya tsinka ba. tattare gashinta tayi tare da dan mai dashi bayan wuyanta kana ta nannaɗe ƙafar wandonta, tsalle tayi tare da kamo rashen da yafi kusa, sai kuma ta hango wasu a can sama haka yasa ta fara taka jikin bishiyar har ta hau bisa rashen duk da ba wani tsowone da shiba, Cal sai gata akan bishiyar. Cikin tsananin takaici da sassarfa ya mike tare da nufar wajen, yasan koda yace zeyi mata tsawa muryarsa baze fita ba saboda bashida da amo mai karfi sannan yasan dai baya cikin tarbiyya mai.kyau ƴa mace tai ta hawe-haween bishi yana isa bakin bishiyar ya tsaya tare da harɗe hannayensa aƙirji kafin yayi magana ta juyo da niyyar kai hannu zata tsinki appel sukayi ido huɗu dashi ido cikin ido sukayi kamar yadda damisa kan iya tsare kenwa da ido haka yayi mata. Cikin tsananin firgici da tsoro da kaduwa tace. “Hasbunallahu wani'imal wakin, Aizubillahi Minal shaiɗanirrajim, innahu min sulaimanu wa innahu Bismillahir rahmanir rahim”. Cikin tsananin tsoro take jera addu'o'in domin gani take shin fatalwane ko kuma aljan yazo mata asuffarsa cikin kiɗima da firgici ta rikito tayi ƙasa ta faɗo gababsa yayin da hannayenta suka sauƙa akan.....! Kada dai ku shagala wannan duk garaɓasar FREE PAGE. Labarin sashi-sashi gareshi. Ko wacce kusufa da darasin dake ƙunshe a ciki. Al'amarin babbane fa babu abinda babu cikin lbrin Inada lbri na musamman Wanda nake son in rubuta in Allah yaso ya yarda ya bani aron rai da lfy da dama. In na gama TUBALI. Zafin labarin kan sani inji Tamkar in aje TUBALI na fara wancan ɗin *SAKAYYAH* lbri ne mai cike da abubuwa na musamman masu tarin rikitarwa al'ajami matsalar kasarmu kalubale masautu. Taraddadin rayuwa, tsaka mai wuya, tsubucewar dama da samunta, Nesanta da kusanta, tausayi, kuka, dariya, barkwamci, iko, isa, mallaka, kasaita, kekkyawan ilimin addini, da aiki dashi, fasadi, zalumci, shirka da sakamonta, kalubalen dalibai ga Malami, matsalar , yadda ya kamata gomnati da jami'an tsaro da masarautun gargajiya su juyo kam lamarin bindiga Dadi Zazzafar soyayya mai kekkyawan tubalin raino a ɓoye!!!. Ya Salam Labarin ya rusa min tunanin da nake cewa bazan sake wani littafi Mai kamar GARKUWA ba sai gashi in second's Allah ya buda min tunanin na harhaɗo Labarin *SAKAYYAH. FATTANAH kenan.* Amman sai dai kuwa kusan wani Abu!??! In kuna son sani ku biya 1k ne kacal 0661110170 GTBank AISHA ALIYU GARKUWA sai ki turo min shaidar biyanki ta WHATSAPP 09097853276. In kin biya kikuma bibiyeni zakusha al'ajab. By *GARKUWAR MARUBUTA* [19/07, 7:44 PM] Halimatu A/rahman Sadeeya: 📝🍇✨💫⏰🤴🏻👹❤️❤️❤️🍇 *SAKAYYAH* _Page 4_ *NA* *AYSHA ALIYU GARKUWA* 🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 *Free page* *KADA DAI KU MANTA WANNAN FREE PAGE NE, KI KI BIYA KI KARANTA CIKIB AMINCI BA HAƘƘIN WANI GABA GAREKI SAKAYYAH 1k ne kacal ƴar uwa. 0661110170 GTBank AISHA ALIYU GARKUWA. Sai ki turo min shaidar biyanki ta WHATSAPP 09097853276* *Al'bishirunku Ma'aurata, GA GARKUWAR KU nan tafe muku da tsarabobi na musamman gareku ma'aurata daga cibiyar mgnin mata mai taken GARKUWAR MA'AURATA* NI DAI AYSHA Ɗiyar ALIYU GARKUWA. Ina matukar mamakin wani irin lokaci da ya riske mu mai wahalallan fassara. Kullum dai magana daya ce, akan ma’aurata, fada, rashin jituwa, mutuwar aure, akan kuskure kalilan, rashin kula, rashin yi wa juna uziri. Toh wai duk me ya janyo hakan? Na zurfafa a tsananin tunani hakan ya tilasta min bincike mai tarin yawa wanda ya kai ni ga gano inda matsalar take? Shin yar’uwa ke macece amma kin san wacece mace ku? Kin san me ake kira mace kuwa? Mace ita ce matar da take zama iyali a wajan namiji ta zame masa bango, sanyin idaniyarsa, ta zame masa gata da farin cikin rayuwarsa ta zame masa ruwa abar kore ƙishinsa ta zame masa mayafi mai karesa daga gigitar kadaici, ta kuma dorar da mijinta kan turbar gaskiya, ta kashe masa jiki da salonta ta rikita shi da baiwa da ni’imar da Allah ya bata idan har ta san hanyar mayar da kanta sabuwa dal awajanta, wato kullun takasance masa tamkar amarya har ya kasa tantance daren amarcinsu da sauran dararen rakun rayuwar su. Wannan ita ce mace. Ina da wata saukakkar hanyar da zaki zama abar so da kulawa da soyayya a wajan mijinki ta hanya mafi sauki, 09097853276 hanyar ita ce ki gwada amfani da kayana na gyara ki gani, ina mai tabbatar miki da in sha Allahu sai kin dara da murna sai kuma kin gode min. Kayana kaya ne da aka yi shi da zallan itacanmu na gado marasa illa a cikin jikin dan adam musamman mace, kaya ne da suke taimakawa (sex hormones 😍) dinki. Misali kina kallon India😘, hollywood, Asian film🥰 kina ganin yanda mazansu ke nunawa matansu tsananin soyayya kamar su ba su kyautar ransu!? Saboda me hakan? Saboda suna sadaukar da lokacinsu wajan gyara jikinsu da kayan da ke tsattsafo da ni’ima cike da tsukewa, kayan nan kuma ana yinsu ne zallar magungunan gargajiya wanda ba su da illa domin haɗine na ingantattun itatuwa da yayansu. Ina baiwar Allahn da miji ke daure mata fuska babu hirar arziki? Zo ki ji yar’uwa zan baki gumbata da zallar gari wanda aka yi su da nagartattun itacen da ke da matukar amfani a jikin mace. Gubar ciko, gumbar tsalle dole, gubar da ba'a baiwa mai kishiya, garin maɗi, garin mallaka, tsumin goron tula, tsumin tsartai, tsumin maratsi, pala-pala butar sirri, kwanon k’asaitacciyar mace, furar mata madararta gareki Hajia takenta sha yanzu mgni yanzu, Ina mata masu fama da sanyi? Sanyin mara ji zo na hadaki da magani na na sanyi wanda yake wanke mara ya fitar da duk wata cuta da ke samun mazauni a wajan set ɗin 10k ne kacal wlh koda sanyin mahaifane in sha Allah zakiji saukin. Ina da ciccibi mai kyau. Ina da hadin amare mai kyau wanda zai gyara yarinya ya kankaro mata kimarta akwai hadin mai jego wanda muke yinsa na asali inada kekkyawan Hadi maida tsohuwa yarinya. Akwai ɗaya bangaren wato *KAMSHI* Kimarki gyaranki da kamshinki. Matan da suka gane suka san yanda za su kankaro da mutunci su ne masu amfani da kayan gyara da kuma sanyaya jikinsu da kamshi, ina da turaren wanka da na bandaki na daki na jiki da na kaya dana tsuguno kamshin turarena na dabam ne mai sanyaya zuciyar wanda ya shaka ina da kayan kamshi na amarya da na maijego da na uwargida da dukkan macen da take kokarin mayar da kanta mai daraja a idon kowa ta zamo sarauni a idon mijinta, akwai shu'umar humra, kana da kulaccar sirri sayan na gari maida kuɗi gida, banda harkar karanta yayin gyara Hajia. Zaku iya samun kayyakina a duk garin da kike, zakiyi min mgn ta whatsApp number na 09097853276 domin yin zaɓinki, ko karin bayani, zaki tura kuɗin ta account na 0005388578 Jaiz bank AISHA GARKUWA ALIYU in mun gama mgna zan sa miki kaya a mota yazo duk garin da kike, in baki shirya saya yanzuba Please kada mu wahal da juna ki bari sai kin shirya kafin kiyi min mgn. 🤝🏻🥰😘 Daga taku AYSHA ALIYU GARKUWA *(GARKUWAR MA'AURATA)* Tana dirowa hannunta dake dungule da Appel suka sauƙa kan ƙafarsa. Yayinda yatsun hannunta dake ɗauke da zoban azurfa na kusa da da ƙaramin yatsa da kuma ƙaramin suka sauƙa akan faratun yatsun sa, atake yatsun hannunta suka bada sautin ƙash! yayin da shi ma Moddibo yatsun ƙafansa suka bada sautin ƙas-ƙas!, Idanshi ya rumtse da sauri, sabida wani irin masifaffen zogi da yaji ya ratsa sa cikin sauri ya tsugunna da niyyan matsasu tuni ɗanƙwalin ta ya zame yalwataccen sumar kanta baƙi daya sauƙa zuwa kafarɗarta ya zubo yana fitar da wani sihirtaccen ƙamshi... Khausar kuwa jin zafin daya ratsa ƙafarta data malkoɗe ne yasa ta furta. “Wayyyo Allah ƙafata!”. ta faɗa da ƙarfi tare da ɗago kanta yayin da yalwataccen sumar kanta ya rufe mata fuska da sauri tasa hannu ta janye ta ɗago kanta. Idanunta ne suka sauƙa akan Moddibo dake durƙushe, cikin ruɗewa da tsanananin tsoronsa ta ɗauki ɗan kwalinta kana ta miƙe da gudu tana cewa. “Innalillahi wa'inna ilahi rajiu'n dan Allah kayi haƙuri wallahi Allah bansani ba”. Ta faɗa tana ƙoƙarin fita daga gate ɗin. Asma'u kuwa fitowarta daga gate ɗin da zai sadaka da cikin farfajiyar Innayi kenan ta hango Khausar na shirin fita babu ɗan kwali akanta. Cikin Sassarfa tabi bayanta tana faɗin. “Khausar! Khausar!! Khausar!!!”. ta kira sunanta har sau uku Kafin ta sake cewa. “Dan Allah kada ki fita ahaka Khausar ki tsaya”. Moddibo kuwa cikin yanayin nutsuwarsa da kuma sanyinsa ya kira sunanta da faɗin. “Asma'u”. Saidai akwai alamun ɓacin rai acikin sautin Muryansa. Atsorace Asma'u ta juya Idanunta cike da tsoro tace. “Na'am Yah Moddibo”. Tsayuwarsa ya gyara tare da lumshe idanunsa masu ƙwarjini da haiba kana ya buɗe su ya dubi Asma'u da har yanzu take tsaye da tsoro a idanunta yace. “Meyesa zaki ɗauko Biri ki kawo mana gida!?”. Ya ƙare mgnar da bin Khausar da ido wacce tuni ta kai bakin gate. Asma'u kuwa saurin ɗagowa tayi ta dubesa jin ya kira Khausar da Biri saidai bata yarda sun haɗa ido ba. Shi kuwa cike da takaici ya cigaba da cewa. “Koda wasa kada ki sake zuwa da wannan yarinyar gidan nan, tunda ita bata da hankali da kuma nutsuwa da kamun kai”. Ya ƙarashe mgnar yana mai lumshe idanunsa dake cike da ƙwarjini har zuwa sannan yatsun ƙafar na masa rawa tamkar alokacin ta buga masa yatsunsa. Ajiyar zuciya Asma'u ta sauƙe ganin tuni Khausar ta fice kanta a ƙasa tace. “Dan Allah kayi haƙuri Insha Allah hakan bazai sake faruwa ba”. Moddibo kuwa baice da ita Komai ba saima lumshe idanunsa da yayi yana motsa laɓɓansa alamar tasbihi yaci gaba da yi. Ita kuwa Asma'u jin baice komai ba yasa ta juya cikin sassarfa ta nufi gate dan bin bayan Khausar... M Jameel dake zaune cikin falon Moddibo kuwa wanda ya tsirawa window idanu yana ganin duk abinda ya faru ya saki lallausan murmushi tare da miƙewa yana gyara zaman Farin t-shirt da blue jeans dake jikinsa kana ya sanya hannu ya buɗe ƙofan falon ya fito fuskarsa ɗauke da ƙayataccen murmushi cikin yanayin sa na ƙaunar Amininsa yace. “Ba sa ido ba?,ka fita sabgar yarinya ka ƙi yanzu inba sa'a ba kasa taji ciwo dan naga lokacin da take gudu tana ɗin gishi”. Moddibo kuwa buɗe idanunsa dake lumshe yayi tare da zab gawa M Jameel Harara cikin yanayin nutsuwarsa daya zame masa jiki yace. “Dama karyewa tayi da shi yafi yarinya bataji bata da hankali ko kaɗan”. Da gudu Asma'u ke bin Khausar tana cewa. “Khausar ki jira ni mana”. Ƙin tanka mata Khausar tayi tana cigaba da sassarfa yayin da ko wani gaɓa na jikinta ke rawa kana tana cigaba da ɗaure gashinta daya baje kasancewar unguwa ce da babu hayaniyar mutane yayin da take yarfe hannunta dake masifar zugi kana tana me ɗingisa ƙafarta. Ganin da gaske Khausar ba zata tsaya ba yasa Asma'u ta ƙara gudunta har ta isa inda take tana sauƙe numfashi saboda gudun da tayi tace. “Ayyah Khausar ki tsaya mana ga hijabinki saka”. Hannunta tasa ta amshi hijabin nata tare da zirashi a jikinta kana taci gaba da tafi. “Ayyah Khausar ki tsaya mana”. Asma'u ta kuma faɗa tare da shan gabanta, a raunane tace. “Bazan tsaya ba Asma'u meyesa zaki min haka Asma'u? banyi tsammanin zaki yimin haka ba gidansu Moddibo kika kawoni mutumin da kin san baya ko son ganina. Gashi yanzu kinsa na buga masa yatsuna masu zobe aƙafa naji masa ciwo,yanzu bansan wani irin hukunci zai ɗauka akaina ba”. Tsoron Khausar ɗaya kada Moddibo yace zai zaneta duk irin rashin ji da ƙiriniyarta tana matuƙar tsoron bulala kana tasan duk hukuncin da Moddibo zai ɗauka bazai wuce yasa Malam Bello ya zaneta idan taje Hadda. Cikin sanyin murya Asma'u tace. “Ayyah Khausar kiyi haƙuri, amman kuma ai da kinji mgnata da haka bai faruba. kece bakya ji sannan ba kyaso ataɓa lafiyar jikinki”. Kallonta Khausar tayi da Idanunta dake cike da tsoro da kuma fargaba tace. “Meyesa zaki ce haka Asma'u kawai naga Appel da inabin ne ya ban sha'awa shiyasa na cira”. Kai Asma'u ta girgiza tace. “Inabi Khausar? na tabbata duk wannan abubuwan da kika gani akwai su a gidanku ku fiye ma da hakan”. Sake Marerece fuska Khausar tayi tace. “Na ganine ya bani sha'awa laifi ne dan na cire!?”. Murmushi Asma'u tayi ganin har zuwa lokacin Atsorace Khausar take sai kuma tace. “Kema dai baki jira kanki ba daga zuwa gidan mutane sai ki fara cire musu abu batare da neman izini ba”. Ita kuwa khausar jin abinda Asma'u tace yasa ta watsa mata Harara cike da tsiwa tace “Tun da kinsan gidan masu baƙin hali zaki je Meyesa zaki ɗaukeni ki kaini?, Kisa aranki daga yau babu inda zan sake rakaki tunda haka kikayi min”. Wara ido Asma'u tayi sai kuma ta langwaɓar da kai tace. “Kiyi haƙuri Khausar bansan haka zai faru ba ni kawai da niyyar mu gaida Innayi nace ki raka ni amma kada kice baza ki sake raka niba na tuba”. Kallonta kawai Khausar tayi amma ba tace komai ba, sake langwaɓar da kai Asma'u tayi cike da tausayinta tace. “Ki zauna awancan dakalin se inja miki ƙafar!” Kai Khausar ta girgiza tana rintse Idanunta tace. “Basai kin ja minba kawai sama mana adedeta mu hau”. Kai Asma'u ta jinjina tare da riƙe hannunta suka ɗan tsaya bakin titi cikin sa'a tsayuwar su babu daɗewa suka samu adedeta hawa sukayi tare da yimasa kwatancen inda ze kaisu... Aƙofar gida me Adedeta ya sauƙe su bayan sun isa Asma'u ce ta ciro kuɗi ta basa kana ta riƙe hannun Khausar suka nufi gate Khausar ce tasa hannu ta tura gate ɗin cikin rashin sani suka buge juna da Samira Sani wacce ke ƙoƙarin fita Amina na biye da ita. Saurin ɗago kai Khausar tayi jin Samira Sani na cewa. Ke 'yar uban waye da zaki haɗa kafaɗa dani shin dame kike taƙama!?”. Kamar Khausar za tace wani abu sai kuma ta fasa taja siririn tsaki tare da jan hannu Asma'u suka bar wajen tana me cigaba da ɗingisa ƙafarta. Ƙwafa Samira Sani tayi cikin kumfar baki tare da tsanan Khausar aranta tace da Amina. “Wallahi na tsani wannan shegiyar yarinyar me kama da sadaka yalla Idan ban sabautata ba bazan taɓa samun nutsuwa ba!”. Tsaki Amina taja tana kallon Samira tace. “Allah ne kaɗai yasan irin abinda zan mata”. Kafin su ƙarasa shiga falon Khausar ta janye hannunta dake cikin na Asma'u kana ta gyara tsayuwar tare da dai-dai ta tafiyarta tana me rintse Idanunta sam bataso Momy ta fahimci abinda ya sameta. Asma'u kuwa kallon ta tayi cike da tausayinta amma batace komai ba Ƙofan falon suka tura suka shiga tare da haɗa baki wajen cewa. “Assalamu Alaikum”. Momy dake zaune kan kujera ta ɗaura ɗaya kan ɗaya ce ta faɗaɗa Murmushin fuskarta tace. “Wa'alaikum salam har kun dawo?”. Zama suka yi daga gefen ƙafarta aƙasan chanis capet Asma'u tace. “Eh Momy”. “Masha Allah ya jikin Innayin?”. Cewar Mommy. Khausar na ƙoƙarin miƙewa tace. “Da sauƙi Momy” Sannan ta nufi Bedroom ɗin ta da sauri Asma'u ta miƙe tabi bayanta. Bakinta ɗauke da sallama tashiga ɗakin nata kana tayi saurin ɗin gisa ƙafarta se kuma ta kwanta agefen gadonta dake shimfiɗe da white bedsheet tana sakin ajiyar zuciya akai-akai alamar har yanzu akwai tsoro atare da ita. Zama Asma'u tayi agefenta ganin yanda ƙafan Khausar ke rawa yasa tace. “Bari na ɗebo ruwan ɗumi na matsa miki”. Kai Khausar ta girgiza da faɗin. “A'a ga can man zafi agaban mirrow ki ɗauka min na shafa”. Kai Asma'u ta gyaɗa kana ta miƙe ta ɗauko man zafin ta ɓude kana ta kama ƙafar Khausar tana mulka mata. Khausar kuwa rintse Idanunta tayi tanajin zafin man na ratsa jikinta yayin da aƙasan zuciyarta tsakanin tsoro da firgicin hukuncin da Moddibo ze ɗauka akan tane. Asma'u kuwa hira ta riƙa yiwa Khausar na ɗebe kewa kana daga bisani ta miƙe ganin yamma tayi seda ta biya ta kichen ta sake yiwa Momy Sallama kana ta tafi. Khausar kuwa yanayin zogin da ƙafarta da kuma hannunta ke mata yasa bayan tafiyar Asma'u ba jimawa bacci ya ɗauke ta... Ita kuwa Momy ganin har maghariba tayi bata jiyo motsin Khausar kuma bata nemi Raudat suyi salla ba se abin ya bata mamaki bayan ta idar da Sallah ta fito daga Bedroom ɗinta Kai tsaye Bedroom ɗin Khausar ta nufa, bakinta ɗauke da sallama ganin Khausar na bacci yasa ta ƙarasa bakin gadon tare da taɓa fuskarta da hannunta dake da damshin ruwa ruwa tana kiran sunanta da faɗin. “Khausar! Khausar!! Khausar tashi kiyi Sallah maghariba tayi”. Momy ke faɗa tana me sake shafa fuskarta da hannunta dake da damshin ruwa. jin muryan Momy da kuma damshin hannunta da take shafa fuskarta yasa ta buɗe Idanunta ahankali tace. “Na tashi Momy”. Juyawa Momy tayi ta fita ita kuwa khausar miƙewa tayi tare da furta. “Alhamdulillah”,Jin babu ciwo da Zugin da ƙafar ke mata se kuma hannun data ji ya sake baki ɗaya tamkar ba ajikinta yake ba. Ta lumshe lumsassun idanunta kana ta miƙe ta nufi toilet tana me furta. “Allahumma Inni Auzubika Minal khubsi wal khaba'is”. Kana tashiga cikin toilet ɗin da komai ke akimtse yana fitar da wani irin ƙamshi Anutse tashiga yin alwalan har ta ida kana ta fito bayan ta furta. “Gufra naka”. Bayan ta gabatar da Salla tayi adduo'i ta miƙe tare da naɗe darduman se kuma ta juya ta fice tana me buɗe hannunta da rufewa koda ze dawo dai-dai... Zaune ta samu Momy kan kujera hannunta riƙe da hisnul Muslim tana Azkharul Masa,Yayin da Raudat ke gefenta daga ƙasa tana bin bakinta zama Khausar tayi daga gefen Raudat kanta aƙasa tace. “Momy gobe zan tafi JAURO YAYAH”. Da mamaki Momy ta zuba mata ido jin mgnar a bakatatam cike da mmki tace. “Zaki tafi Jauro yaya kuma Khausar?”. Ataƙaice Khausar tace. “Eh”. tana mai cigaba da jan yatsun hannunta. Momy ta sake duban ta da mamaki akaro na biyu tace. “Anma babu yanda banyi dake ba jiya kan cewa kishirya yau kutafi tunda mutanen garinsu na zuwa sallan jumma'a sosai ku tafi tare, kika ce ba zaki tafi dasu ba kuna hadda, sannan kun kusa zuwa ƙarshen surar idan kika tafi karatun ki ze koma baya sannan na yarda na barki kan cewa se sati me zuwa yanzu kuma kice zaki tafi gobe”. Murmushi ta ƙaƙalo tare da faɗin. “A'a Momy babu damuwa munyi magana da Asma'u tace koda awaya zan iya ƙarawa da kaina batare da anwuce Ni ba”. Dubanta Momy tayi tare da cewa. “Kin tabbata Khausar har cikin ranki kikeson zuwa Jauro Yaya!?”. Kai ta gyaɗa tace. “Eh”. Aranta kuwa cewa tayi ba gwara masifar wancan tsohuwar ba dan ko yaya bazan tsaya ta dake niba amma wannan mutumin ya riƙa tsareka da firgitattun idanunsa masu saka tsoro da fargaba, baya ga haka in banyi sa'a ba duka na zai sa ayi banyi masa lefi bama idan yasamu sarari sawa yake aci zalina bare kuma nayi masa laifi... Muryan Momy dake cewa. “Toh shikenan nima nafi so ki tafi Kinga idan hutun ku ya ƙare sannan anƙarasa muku gyaran makaranta seki dawo”. Ya dawo da ita daga duniyar data lula. Kai ta gyaɗa tare da cewa. “Shikenan Momy”, Sannan ta miƙe ta shiga Bedroom ɗin ta. Momy kuwa Hisnul Muslim ta ɗauka ta cigaba da Azkhar yayin da Raudat ta miƙe tabi bayan Khausar. Ita kuwa khausar na shiga ɗaki ta hau kan stoll ta janyo trolley ɗin ta sannan tashiga haɗa kaya Raudat dake kallonta tace. ”Dani Zaki tafi Addah Khausi?”. Girgiza mata kai Khausar tayi alamar a'a. Kuka Raudat ta fashe dashi tana cewa. “Ni zan biki”. Zama Khausar tayi ta riƙe hannunta tare da langwaɓar da kai tace. “Raudat garin bashi da daɗi fa, ga tsohuwar garin ta fiye masifa, kana yi mata kuskure kaɗan zata zane Mutum”. Jin haka yasa Raudat ta girgiza kai tace. “Nide ba zanje ba idan haka ne”. Aɓangaren Momy kuwa bayan tashiga turakar Lamiɗo sunyi shirin kwanciya ta dubesa fuskarta ɗauke da murmushi me sanyi tace. “Uhum wai ɗazu Khausar ke cemin idan Allah yakaimu gobe tana son zuwa Rugar Jauro Yaya”. Zamanshi ya gyara tare da faɗaɗa Murmushin dake fuskarsa kana yace. “Allah ya kaimu hakan nada kyau idan yaso tunda gobe weekend ne zamuje dukan mu kema sai ku gaisa tunda kinyi shekaru baki jeba”. Kai ta jinjina kafin tace. “Kai naji dadi Allah ya kaimu”. Amin yace kana sukaci gaba da hirarsu. Washe gari Ya kama asabar da wuri Khausar ta tashi ta gyara ɗakinta sannan ta nufi ɗakin Momy ta gyara kana ta share har zuwa falo da kuma duk sashen saida ta gyara ko wani lungu da saƙo. Bayan ta gama ta dawo ta shiga kichen ta zuba musu Breakfast soyayyan cheaps da tea ita da Raudat ke ciki. Bayan sun kammala ta miƙe tana ƙoƙarin tattare wajen Momy tashigo Idanunta akan Khausar. fuska ta ɗan tsuke tare da faɗin. “Maza kije yanzu Aunty Jamila tayi Miki kitso”. Aunty Jamila matar ƙani Lamiɗo ne sannan Momy tasan inba tayiwa Khausar dagaske to baza taje ba domin bata ƙaunar kitso. Ganin fuskar Momy babu walwala yasa Khausar gyaɗa kai tare da shiga Bedroom ta ɗauko dogon hijabinta fari Nevy blue daya sha ninkin guga ta ɗaura akan riga da wandon dake jikinta kana ta fice ta nufi gidan Aunty Jamila tana zumɓura baki da kuma kifiya da kum a hannunta. Bakinta ɗauke da sallama tashiga gidan, Aunty Jamila dake zaune ta amsa Sallamar tana faɗaɗa fara'ar dake fuskarta tace. “A'a Khausar kece?, sannu da zuwa”. Sake fuska Khausar ta ɗanyi tace. “Eh nice Aunty wai kitso nazo kiyi min zanje Jauro Yaya”. Murmushi Aunty Jamila tayi tare da cewa “Masha Allah kice zakije ziyara?”. Kai Khausar ta gyaɗa tana murmushi. Cikin sakin fuska Aunty Jamila tace. “Allah Ya kaiku lafiya". “Amin ya rabbil izzati”. Cewar Khausar. “Kinga kuwa kinyi sa'a duk na gama aiyuka na”. Da sauri tace. “Aunty Jamila manya fa zakiyi shida ko takwas”. Murmushi Aunty Jamila tayi. Kana ta miƙe ta shiga ɗaƙi tare da kwantar da yaronta kana ta fito, Akan kujeran roba Khausar ta zauna ita kuma ta tsaya ta fara yi mata kitson suna cikin kitson ne suka jiyo Sallamar Gimbiya Dadu. Anutse Aunty Jamila ta ɗago kanta fuskarta ɗauke da murmushi tace. “Sannu da zuwa Mama”. Asaman laɓɓa Gimbiya Dadu ta Amsawa Aunty Jamila baki ɗaya nutsuwarta da hankalinta suna kan Khausar. Miƙewa Aunty Jamila tayi tashiga ɗaki dan ɗaukowa Gimbiya Dadu Darduman zama. Ita kuwa khausar ahankali ta ɗago kanta caraf Idanunta suka sauƙa akan Gimbiya Dadu data tsareta da ido ita kuwa khausar cikin hanzari tayi ƙasa da idanunta tana mai karanto duk wata addu'ar da tazo bakinta kamar minti ɗaya Khausar ta sake ɗago kanta akaro na uku still Idanun Gimbiya Dadu na kanta. Ita kuwa khausar kasa jurewa tayi ta tsayar da Idanunta akan Gimbiya Dadu cikin dakiya tace. “Wai dan Allah Gimbiya Dadu Meyesa kike kallona haka?”. Wani murmushi mai cike da ma'anoni Gimbiya Dadu tayi tare da cewa. “Uhum yaro man kaza, ai tunda kika bar cikin Awaki 'yan uwanki kika dawo cikin Kuraye ai dole akalleki! In kalleki in kuma”. jin abinda Gimbiya Dadu tace yasa ta miƙe cikin rawan jiki da alamar tsoro aƙwayar Idanunta ta sanya hijabinta ta fita batare data jira Aunty Jamila ta fito ta ƙarasa yi mata kitson ba... Sauri-sauri gudu-gudu take tafiya har ta isa bakin gate dinsu da sassarfa ta shigo coumpund ɗin su har yanzu jikinta be daina ɓari ba tana gyara zaman hijabin kanta Momy ta fito,Kallonta Momy tayi tare da cewa. “Har angama kitson ne". Ka ta gyaɗa mata ba tare da tace komai ba. “Dama yanzu zan aika Haiydar ya kira ki kizo mu tafi”. Murmushin karfin hali ts ƙirƙira kana tace. “Eh mun gama”. Wuce ta Momy tayi taje tashiga gaban mota Ita kuwa khausar kallon Raudat, Ramadan, da kuma Haiydar dake tsaye tayi tare da ɗaga musu hannu suma hannu suka ɗaga mata ahankali ta juya ta nufi wajen motar tana isa tasa hannu ta buɗe tashiga gidan baya Haiydar da Ramadan na cigaba da ɗaga mata hannun. Babban gate mai gadin ya buɗe musu kana Lamiɗo ya cilla hancin motarsa. Khausar kuwa jingina bayanta ajikin motar tayi tare da lumshe Idanunta zuciyarta na bugawa da mugun sauri abu biyu ne suka yiwa zuciyarta ƙawanya na farko hukuncin da Moddibo zai ɗauka akanta na biyu kalaman Gimbiya Dadu wanda suke ƙara tabbatar mata da zantuka dake yawo a gari cewa matar nan mayyace... Anutse Momy ta dubi Moddibo dake sharara gudu akan Lafiyayyan titin nasu tace. “Abban Haiydar gudun nan baiyi yawa ba”. Kanshi ya ɗan jujjuya mata, Ita kuwa cikin sanyi tace. “Gsky dai ka rage gudun kamar yayi yawa”. Juyowa yayi ya kalleta da murmushi a fuskarsa yace. “Lokaci na tafiya kinga yanzu goma tayi gwara mu isa da wuri kada rana tayi mana mu samu mu juyo da wuri”. Kai ta gyaɗa kafin tace. “Amma duk da haka arage gudun". Tattausan murmushin ya sakar mata tare da gyaɗa kai... Sunyi tafiya mai tsawo kafin suka fara hango garin Atake suka fara tabbatar da sanyin da ake acikin Gembila wasa ne. Domin tun kafin su shiga garin suka hango tamkar hayaƙi ke tashi saboda masifaffen sanyin da ake tsugawa acikin Jauro yaya suna shiga cikin garin suka fara ratsa bishiyoyi masu korayen ganye suna rangaji tare da fitar da sanyayyan Iska kasancewar hantsi ne duk makiyaya sun tafi se kuma, 'yan dalo da aka ɗaɗɗaure masu kyan launi ga kuma kukan tsuntsaye dana zabbi da ke tashi suna ajiye ƙwai. Suna shiga tsakiyar Rugar Jauro, kai tsaye ƙofar gidan dake kusa da babbar fadan Rugar suka nufa anan sukayi parking motar tare da fitowa. Wasu dattawa dake zaune aƙofan masallacin dake kusa da babbar fadan suka taso baki ɗaya idanun su akan Khausar data fito daga mota tana gyara zaman hijabinta suna faɗin. “Audiii Barka da zuwa kece?”. ɗaya daga cikin dattijon ne ya taso wanda ya kasance shine Jauron garin ya riƙe hannun Khausar. Fuskarsa ɗauke da murmushi yake faɗin. ”Addah, Addah, Addah, kizo ga Khausar”. sauran ma bin bayansu sukayi zuwa cikin gidan suna masuyiwa Momy da Lamido Barka da zuwa. Biyu daga cikine suka ce da Momy da kuma Lamiɗo. “Sannunku da zuwa ya kuka tsaya ku shigo daga ciki”. Kai Momy ta gyaɗa kana suka yi musu godiya bisa jagoranci suka nufi cikin gidan. Jauro kuwa yana riƙe da hannun Khausar yana mata wasa da faɗin. “Iyeee girman falo ji jiki kamar auduga, bakisan riƙe sandar kiwo ba sannan baki san ta tsar nono ba girman burodi wayon shayi kawai”. Ita kuwa khausar hannu ta wara da faɗin. “Ban iya ba kam”. Murmushi yayi kana yace. “Zamu koya muki ai”. maƙale kafaɗa tayi tace. “Bana so ba kace min girman bread wayon tea ba”. Murmushi yay i tare da cewa. “To girman fura da nono”. Akuma dai-dai lokacin suka shiga ɗakin tsohuwar wanda yake ginin gargajiya shatin kobo. Suna shiga Jauro yace. “Addah ga 'yar Usman tazo”. Ya mutse fuska Hajja Nana tayi tare da kallon Khausar tace. “Shegiyar kaya me wuyar ɗauka se yau kika ga damar zuwa??”. Murmushi Jauro yayi still hannunsa na cikin na Khausar yace. “Tazo da mahaifiyarta da kuma Mahaifinta”. Wani kallo Hajja Nana ta masa tare da cewa. “Kai Jauro ka gyara kalamanka, badai mahaifinta ba mahaifin riƙo dai ko? ka manta mahaifinta da kai aka binnesa shekaru goma sha biyar da suka wuce?”. Kai ya jinjina alamar hakane amma bece komai ba ita kuwa miƙewa tayi ta ɗauko taburma ta shimfida tare da ɗauko darduman kilisa ta shimfiɗa. A kuma lokacin Momy da Lamiɗo suka shigo cikin sakin fuska tashiga yi musu lale marhaba. zama Momy da Lamiɗo sukayi akan shimfiɗar data musu kana ita kuma ta zauna awajen zamanta na farko yayin da duka ƙannenta maza suka zauna daga bayanta se ta zamto tamkar sarauniya acikinsu ko wannensu fuskarsa ɗauke da murmushi yake faɗin. “Addah yau kam ga Khausar tazo”. Haka yasa ta juyu. Ta dubi Khausar da alamun farin cikin ganinta afuskarta saidai yanayin zafinta bazai sa ka fahimta ba. Ta dubi Khausar da tayi kicin-kicin da fuska tace. “Menene kike wani kumbura fuska? gwara ma ki saki ranki fa”. Zumɓura baki Khausar tayi saidai ba tace komaiba. Hajja Nana kuwa sake kallon Khausar tayi akaro na barkatai tace. “Ki tashi ki kawo ma baƙi abin taɓawa”. Lumshe idanu tayi kafin tace. “Nice zan kawo abin taɓa wa?,Nima ai baƙuwa ce akawo mana dai”. “Ina magana kina magana!?”. Hajja Nana ta fadi a faɗace. Cikin tura baki tace. “Ai gaskiyane”. Danƙolo Momy ta yiwa Khausar hakan yasa ta tsuke bakinta. Ɗaya daga cikin ƙannen Hajja Nana wanda ya kasance shine ƙaramin su (Autah)ya miƙe da faɗin. “To bari na kawo musu”. Sannan ya shige uwar ɗakan Hajja Nana ba daɗewa ya fito hannunsa riƙe da Akwashi ya ajiye agabansu sannan ya koma ya ɗauko goran zuma kana ya koma ya sake ɗauko wani Akwashin. Hajja Nana ta dubi Momy tare da cewa. “Ayyah wallahi ban san da zuwanku ba”. Kai Momy ta gyaɗa tare da cewa. “Ai inata gwada kiran layin ki baya shiga”. Murmushi Hajja Nana tayi kana tace. “Kinsan Rugar tamu bamu da network se kaje bishiyar ƙare zancenka in kaje bishiyar ma seka hau sama ni kuma ban cika son zuwa ba da girmana Inje in hau bishiya na faɗo”. Khausar kuwa taɓe baki tayi tace. “Hmmm ba network kuma har sai anje wani bishiya?”. Harara Hajja Nana ta watsa mata ta cigaba da cewa. “Wallahi bansan da zuwan kuba dana shirya muku abin taɓa wa”. Murmushi Momy tayi batace Komai ba. Akwashin da aka shigo dashi ne Autansu Hajja Nana ta buɗe Nono ne me zafi yana tururi ga kuma goran zuma dake gefe ɗayan kuma daya buɗe ɗumamen danɗerun zabbi ne suna tururi. Sauran mazan dake kewaye da Hajja Nana ce suka shiga Gaisawa dasu Lamiɗo. Muskutawa Hajja Nana tayi tare da gyara zamanta ta kalli Lamiɗo dake zaune ya tanƙwashe ƙafafunsa tace. Wa'annan daka ke kallo duka ƙannena ne mu goma ne acikin mahaifiyarmu gaba ɗayansu Mazane ni Kaɗai ce mace kuma nice 'yar Fari. Jinjina kai Lamiɗo yayi yana sauraronta da duka nutsuwarsa duk da yasa abinda take faɗa kishin. tunda ba yaune zuwansa na firkoba. Ita ko Hajja Nana nuna wanda ke gefenta tayi tare da cewa. “Ga mai bina Jauro, Sannan kuma sai Sadu, Sannan se Abubakar, Sai kuma Garga, sannan sai Aliyu liman, Sannan kuma sai Dumau ,Sai Salmanu, Sannan kuma Isa sai kuma Umaru”. Lamiɗo kuwa kallon su yake yana sake tabbatar da abinda ta faɗa saboda kamannin dake tsakanin su. Hajja Nana tayi murmushi tace. “Duk ƙanne nane sannan kuma duk da matansu”. Ta nuna Jauro tace. “Matan sa biyu,Garga ma Matansa biyu, Sannan Sadu ma matansa biyu, sai kuma Liman shima Matansa biyu”. Ta sake nuna Jauro, Sadu, Garga, da kuma Liman tace. Jauro da Sadu 'ya'yansu maza biyu sunyi aure kuma 'ya'yan Liman da Garga suka Aura ma'ana Auran dangi sukayi”. Lamiɗo kuwa murmushi yayi alamar yana fahimtar abinda take faɗa masa. Ita kuwa Hajja Nana cigaba tayi da cewa. “Duk garinmu babu bare mu ya mune, sannan kuma babu maye mu garinmu atsarkake yake kushigo hankalin ku kwance ku fita lafiya, Salamun Ƙaulan Min rabbil Raheem”. Momy kuwa sunkuyar da kai ƙasa tayi Saboda tasan ana zargin Mahaifiyar Lamiɗo da Maita. Shima Lamiɗo sun kuyar da kansa ƙasa yayi dan yasan zargin da ake yiwa Mahaifiyar sa kenan kasancewar sa mutum me haƙuri da kuma dattako saiya ɗago kansa fuskarsa ɗauke da murmushi yace. “Masha Allah yayi kyau zuri'a tayi albarka Allah yaƙara rufa asiri”. Murmushi Hajja Nana tayi tace. “Ameen ya Allah”. Domin Hajja Nana 'yar takife ce bata tsoro inma tsoron wani abu ake itace ke isar dashi. Miƙewa Sauran sukayi suna kallon Lamiɗo suka ce bari mu barku kuci abinci sannan suka fice. Itama Hajja Nana miƙewa tayi tace. “Khausar zo mu shiga ciki kici naki”. Girgizi kai Khausar tayi tace. “A'a zanci anan”. Ta juyi ta dubi Khausar da kyau tace. “Kizo mu tafi nace”. Shi kuwa Lamiɗo cike da ladabi yace. “Da kin barta munci anan ɗin babu matsala”. Juyawa Hajja Nana tayi kafin tace. “Toh shikenan”. Miƙewa Khausar tayi tabi bayanta ta karɓo ƙananan akwashi aka zuba mata sannan suma suka zuba,Yanayin sanyin da ake tsugawa agarin yasa mazauna garin ke bukatar abu me ɗumi,Suna cin zabbin suna ɗaurawa da Nono me ɗumi bayan sun gama Khausar ta miƙe ta tattara akushin ta mayar. Ganin ta mayar ne yasa Hajja Nana fitowa suka zauna. Atake sega yara suna ta shigowa a jere a jere angama abincin rana suna kawowa duk gida Jen garin Hajja Nana tana da kwanonta acan suna kawo mata abinci domin ita bata girki abinci safe ne kawai bata Yarda akawo mata ita take dafa wanda zata ci,Duk ƙannenta taran nan sai ankawo kwanuka tara an ajiye mata ga kuma na 'ya'yansu da sukayi Aure tana da ƙore goma sha uku. Ga yaran garin ƙanana kyawawa dasu farare soll kamar irin yaran ƙauyen larabawa. Lamiɗo da kansa da yaga yaran na shigowa sun basa sha'awa,Ko wacce idan tashigo zata ce. “Goggo Hajja! Goggo Hajja!! Aɗonna”. Ƙannenta da Addah Nana suke kiranta 'Ya'yan ƙannenta kuma Goggo Goggo Hajja idan kuma jikoki zasuce mata Hajja Nana. Duk Wacce ta kawo mata abinci zata ce nice,daga gidan Sadu,Nice daga gidan Garga,saboda yawansu kowa ke gabatar da kansa. Duk wanda yazo ya ajiye zata ce. “Angode masu nomawa Allah ya basu ƙarfi da lafiyar nomawa masu girkawa ma Allah yabasu ƙarfin girkawa”. Sannan ga yanayin tsarin yaran garin babu alamar ƙazanta ajikinsu ko wanne tsaf dashi ga kuma tarbiyya duk wanda suka zo sai sun tsugunna sun gaida Lamiɗo da Momy da fulatanci kasancewar basu iya Hausa Sosai ba. Ɗaya daga ciki data zone ta ajiye kwanon Idanunta akan Khausar tace. “Goggo Hajja Khausar naa” . Murmushi Hajja Nana tayi tace. “Eh”. Murmushi yarinyar tayi ta matso kusa da Khausar tace. “Sunana Dija”. Murmushi Khausar tayi tace. “Yayi kyau Dija”. Dija ta kuma murmushi tace. “Kullum Goggo Hajja na bamu labarin ki rabonki da nan tun kina ƙarama yanzu ya kai shekara shidafa ake cewa”. Kai Khausar ta jinjina da faɗin. “Eh”. Hannunta Dija ta riƙe tace. “Kizo muje gidanmu ku gaisa da Mamana”. Ta ƙare mgnar tare da jan hannu Khausar suka fice... Kiran sallan Azahar yasa Lamiɗo ya miƙe ya tafi masallaci tare da Ƙannen Hajja Nana ita kuma Momy tayi alwala tare da gabatar da sallah bayan sun idar da Sallah Hajiya Aysha ta ɓude jakan da tazo dashi ta fito da turaman zannuwa da Sabulai ta miƙawa Hajja Nana. Murmushi Hajja Nana tayi tace. “Hadda ɗawainiya haka?,To angode Allah yayi albarka”. “Ameen”, Momy ta amsa kafin tace. “Hajja ga Khausar nan na kawo tayi hutu amma mako uku ne hutun nasu”. Murmushi Hajja Nana tayi tace. “Toh Nagode”. Ita ko Momy tana gyara mayafinta tace. “Sati uku ne hutun nasu”. Faska Hajja Nana ta tsuke tare da cewa. “Sai kin sake Jaddada min ne?”. Da sauri Momy ta girgiza mata kai. Cikin isa tace. “Toh sai sanda naga dama zata dawo kinyi naki saura nawa”. Ƙasa da kai Momy tayi tare da faɗin. “Shikenan Hajja duk yanda kikace yayi mukan zamu tafi”. Miƙewa Hajja Nana tayi tace. “Bari akira muku Khausar kuyi sallama”. Cike da ladabi Momy tace. “A'a Hajja base ankira taba”. Dan tasan muddin aka kirata sai tayi kuka kafin su rabu. Sallama suka sake yi musu kafin suka fice suka tafi... Acan Gembila kuwa Washe gari. Asabar Moddibo ya shirya kamar ko yaushe cikin Jallabiya Sky blue Kansa sanye da hula da kuma hirami cikin nutsuwarsa kamar ko yaushe ya shiga cikin makarantar yana motsa laɓɓansa alamar tasbihi da hannu kawai yake amsa gaisuwar da ɗaliban haddar ke masa kai tsaye Ajin haddarsu Khausar ya nufa yayin da Aransa yayi ƙudurin sawa Malam Bello ya casa masa ita saboda gaba ta kiyaye domin ya lura ganganci da sakalci ke damunta. Cikin rashin sa'a yana shiga ajin ya samu bata nan. Asma'u ya kira. Cike da ladabi ta fito tare da tsugunnawa agabansa tace. “Gani Yah Moddibo”. Tsayuwar sa ya gyara cikin yanayin sanyin Muryansa yace. “Ina wannan Birin?”. Asma'u kuwa kanta aƙasa tace. “Nima yau da nazo ban ganta ba sai nake tambayar Amina ina take shine tace wai taje garin Kakanninta”. Ƙwafa yayi yace. “Shikenan yayi kyau”. Kana ya juya ya bar waje.... Acan mota kuwa Momy ta dubi mijinta tace. “Kayi hakuri da Hajja Nana yanayin tsufa ne”. Murmushi yayi still Idanunsa ahanya yace. “Ai bakomai ba gamu da Gimbiya Dadu ba ai haka take”. Acan Rugar Jauro yaya kuwa bayan Khausar ta dawo gida ta tar da Momy ta sun tafi ta tsare Hajja Nana da ido tace. “Meyesa ba ki kirani ba kafin su tafi?”. Salati Hajja Nana ta sanya tace. “Tuhuma ta kikeyi? Ko kuma me?”. baki ta cinna sama tare da cewa. “Ai gaskiyane abinda ya dace na faɗa”. Salati Hajja Nana ta sanya tare da faɗin. “Ohhh ni Shatu Allah ya nuna min 'yar Usmanu yarinya kamar ruwan aski sai rashin ta ido”. Ta ƙare mgnar tana kallon Khausar dake tsaye fuska akumbure cikin tsawa tace. “Bari kiji in faɗa miki ni agarin nan idan nayi magana kamar yankan wuƙa yake babu me bani Amsa ko musu ko jayayya dani!”. Ita kuwa Khausar wani irin juya Ido sama tayi tare kana tace. “Uhummm to gwara ma ki sani. Idan maganarki yankan wuƙa ne to kin samu me yankan rez”......! Littafin SAKAYYAH na kuɗine biya ki karanta 1k ne kacal 0661110170 GTBank AISHA ALIYU GARKUWA By *GARKUWAR MARUBUTA* [19/07, 7:44 PM] Halimatu A/rahman Sadeeya: 📝🍇✨💫⏰🤴🏻👹❤️❤️❤️🍇 *SAKAYYAH* _Page 5_ *NA* *AYSHA ALIYU GARKUWA* 🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 *FREE PAGE* *LITTAFIN SAKAYYAH NA KUDINE, 1K NE KACAL ki biya ki karanta cikin Aminci ba haƙƙin wani a kanki. 0661110170 GTBank AISHA ALIYU GARKUWA, sai ki turo min shaidar biyanki ta WHATSAPP 09097853276.* Zare Ido Hajja Nana tayi cikin faɗa da fushi tace. “Ke! Ke!! Ke!!!.Faɗimatu ki kiyayi kanki dani fa zan tsige Miki fuka-fukinki!”. Ita kuwa khausar fuska ta haɗe Idanunta tsaye akan Hajja Nana tace. “Nifa ba tsuntsuwa bace da zaki tsige min fuka-fuki, ai gaskiyane tsakani da Allah da Annabi mahaifiyata zata tafi kinsa ankawo ni aise ki kirani muyi sallama na musu Allah ya tsare”. Ta ƙare mgnar tare da juyawa ta kalli Dija tace. “Fisabillilhi ba haka ya kamata ba Dija?”. Dija kuwa tuni ta sunkuyar da kanta yayin da jikinta ya shiga ɓari tsananin tsoro ya bayyana afuskarta sanin halin Hajja Nana babu wanda ya isa tana magana yana mayar mata da martani!. Cikin rawan jiki da tsoro daya bayyana amuryanta tace. “Khausar kidena kar ki sake bata amsa ki bata haƙuri”. Tana ida maganar ta tsugunna gaban Hajja Nana tace. “Goggo Hajja Waɗɗu munyal”. Hajja Nana kuwa kwaffa tayi kana tace. “Aaaa Dija matsa kusa da ita inzo na same ta ai ke ba ruwanki”. Ita kuwa khausar batare da tsoro ba tace. “Toh kizo mana kawai dan mutum ya faɗi gaskiya don dai ba'a son gaskiya da zaman lafiya ai yakata dai akirani muyi sallama da Momyna tunda dai ansa an kawoni wataƙila ma sai nayi sati biyu ko uku bangan taba aida se akirani muyi sallama ince agaida mutanen gida sannan nayi musu fatan isa gida lafiya”. Ita kuwa Hajja Nana afusace tace. “To idan kece zaki kaisu gida lafiya kada Allah yasa ki kaisu shegiyar yarinya mara ji Ɓee Usmanu La'ilaha illallahu ohoho gabtarel”. Tuni Baffa Jauro da Baffa Sadu suka shigo idanun su akan yayar tasu suka ce. “Lafiya Addah Hajja?”. Kai ta girgiza tare da nuna Khausar dake cika tana ba tsarewa tace. “Ɓeee Usmanu,Nikam ban taɓa ganin fitsararriyar yarinya kamar 'yar Usmanu ba”. Itade Khausar na jingine jikin bango tana tura ƙaramin bakinta dake ƙarawa fuskarta kyau. Kallon ta Hajja Nana tayi cikin harara tace. “Nikam Usamanu na Kam ba haka yake ba, haka zalika Mahaifiyarki ko surukata ce bazan mata ƙazafi ba macece mao mutunci amma ke kam waya fitsare miki Ido? Kodan zama tsakiyan Mayun gidan kune yasa kika zama haka!?”. Khausar dake jingine da bango ta ɗago kanta kana ta wara manyan Idanunta masu kyau da tsari tace. “Nikam de kar kice min Mayya idan su Mayu ne toni ba Mayya bace idan kince ni Mayyace sede idan awajenki na gada!”. Baffa Jauro da Baffa Sadu suka dubi juna alokaci ɗaya cikin ƙasa da murya yanda Hajja Nana ba zata jiba Baffa Jauro yace. “Lalle akwai rigima anan? Addah Hajja ba abata amsa idan tayi magana amma ga 'yar Usmanu daga zuwa tana bata amsa gatse-gatse jika kenan mafi akasari duk zafin mutum jikoki bazasuji tsoronka sosai ba”. Murmushi Sadu yayi yana jinjina kai. Baffa Jauro kuwa kan Khausar ya ɗan buga yace. “Kay Hausajo kidena mu ba'a rashin kunya agarin nan!”. Ita kuwa khausar inda ya ɗan bugeta tasa hannu ta riƙe tana sosawa duk da cewa bawai zafi ya mata ba ta tura ƙaramin bakinta tace. “To ai muma ba rashin kunya bane wannan kam”. Dan ƙolo ya mata yace. “Dije jata ku tafi”. Kai Dije ta gyaɗa wacce se alokacin ta samu kuzarin miƙewa tace. “Khausar kizo mu tafi“, Sannan taja hannunta suka fita. Suna fita Khausar kuwa hannunta dake cikin na Dije ta janye tace. “Yanzu ina zamuje?”. Murmushi Dije ta sakar mata tace. Rafi zamuje”. Murmushi mai sanyi Khausar ta sakar mata wanda ke ƙarawa fuskarta kyau tace. “Toh mu tafi”. Dan sosai weather garin yake abin burgewa da sha'awa. Cikin nutsuwa suka nufi Rafin suna hira. Da sauri Dije ta riƙon hannun Khausar tare da nunawa mata gefen damansu, masu wasa da birine ke tafiya kana yaran rugagen dake gefe dasu na biye dashi, bisa alamun yanzu kuma rugarsu zasu shiga. wani ƙaton Biri yake ta kolongoiso yara nata ja da baya. Cike da nishaɗi Khausar tace. “Muje muma mu gani”. Kai Dije ta gyaɗa mata , kana suka nufi wajen me wasa da Biri suna ganin yanda Birin ke duk abinda aka sashi. Cike da farin ciki Khausar ta kalli mai wasa da Birin tana ƙara kusawa cikin yara matan tace. “Mai Biri yanzu duk abinda na sashi zai min?”. Kai mai wasa da Birin ya jinjina yace. “Idan kuma baki yarda ba ki gwada ki gani”. Kusa da Birin Khausar ta matsa tana murmushi tace. “Yauwa yaya salon mugun Malami yake idan zai daki ɗalibansa?”. Da sauri ta ware idanunta ganin. Birin ya wani ja baya tare da harɗe hannunsa aƙirji kana ya ɓata fuska tare da harɗe sawunsa sai kuma ya ɗauki wani sanda ya riƙe yana nuna Khausar da Dije. Hannu Khausar tasa ta dafa kafaɗar Dije tare da tintsirewa da dariya mai cike da sautin shauƙi yayin da ɗaya hannun kuma ta ɗaura saman shafefen cikinta tana mai cigaba da dariyar. Domin kuwa babu wanda ya faɗo mata arai lokacin da Birin ke gwadawa face Moddibo duk da kasancewarsa ba mutum ne mai Fara'a ba amma duk sanda zaisa a zaneta a makarantar Islamiyya seya sake tamke fuskarsa.. Dariya sosai takeyi wanda da yawa cikin yaran tayata sukeyi. Ganin bata da niyyar daina dariyar ne yasa Dije jan hannunta cikin dariya tace. “Khausar Mu tafi,Dariyar me kuma kike haka!?”. Tsagaita Dariyar Khausar tayi sai kuma lokaci ɗaya jikinta yayi sanyi tuna wa da tayi Moddibo zai iya jira duk lokacin da tawo ya yanke mata hukunci ahankali tace. “Kawai na tuna da wani Malamin mune”. Murmushi Dije tayi tace. “Allah sarki shike zaneki kena”. Kai ta jujjuya tare da cewa. “Wancan da shegen madarar ƙasaita sawa yake a zaneni dai yana nan jiki kamar auduga ai shi dukan ma aikine a wurinsa”. Murmushi Dija tayi tare da cewa. “Da Goggo Hajja zataji haka sai ta sa mishi al'barka”. Baki ta tura ba tare da tace komai ba sukaci gaba da tafiya. Suna shiga Rafin idanun Khausar ya sauƙa akan Bishiyoyin Piya, Caɓɓulle, Mangoro, Ayaba, Gwanda, Gwaba, Lemo, da sauran kayan itatuwa duk sun yiwa wajen ƙawanya. Sake wara Ido Khausar tayi ganin bishiyoyin Inabi guda uku a jere, Cikin farin ciki ta dubi Dije tace. “Harda Inabi Laha'Ila Ha'illalhu Masha Allah zan kuwa ci”. Ta ida maganar tare da nufar jikin Bishiyar zata hau. Saurin riƙe hannunta Dije tayi tace. “Kada ki hau Khausar Baffa Liman ya hanamu yace ba shida amfani 'ya'ya mata su riƙa hawa bishiya ba tarbiyya bace mai kyau”. Ita kuwa khausar janye hannunta dake cikin na Dije tayi tace. “Ke rabu dashi da ƙa'idojinsa hawa za muyi mu cire abinmu, ai kuma ba har can sama zamu hauba”. Langwaɓar da kai Dije tayi kafin tayi magana suka hango wani farin saurayi kyakkyawa daga ɗaya gefen. Hannu Dije ta ɗaga masa da faɗim. “Yawwa Sadik dan Allah zoka cire mana Inabi wai zata ci”. Ƙara sowa Sadik yayi idanunsa akan Khausar yace. “Dije wannan yarinyar wa kika samo?”. Murmushi Dije tayi tace. “Yarinyar Marigayi Baffa Usmanu cefa yaron Goggo Hajja”. Murmushin fuskarsa ya faɗaɗa yace. “Allah sarki itace wacce take Birni ko?”. Kai Dije ta gyaɗa tace. “Eh itace”. Ita dai Khausar ba tace komai ba. Raɓar bishiyar yayi ya ciro musu Inabi kana ya koma bishiyar Ayaba shima ya ciro yasa musu aƙaramin kwandon dake hannunsa irin na saƙar kaba na gargajiya miƙawa Dije yayi. Sai asannan Khausar tace. “Mungode”. Murmushi kawai yayi ba tare da yace komai ba, suka fara tafiya cikin rafin akai-akai Khausar ke lumshe idanunta tana wasa da yatsun hannunta sosai weather garin ya mata daɗi. Juyowa tayi ta kalli Dije tare da cewa. “Garinku yayi min daɗi”. Cikin sauri Sadik yace. “Garinmu de kin cire kanki ne a ciki? Ko kin manta nanne tushenki kuma asalinki nanfa cibiyarki take abinne”. Dariya tayi kafin tace. “Hmmm Shiyasa ma naji daɗin garin inba haka bama masifar wannan tsohuwar yasa bana sha'awar zuwa garin nan”. Zare ido Sadik yayi yace. “Wacece masifaffiyar!?”. Asanyaye Dije za tace. “Wai Goggo Hajja take cewa masifaffiya”. Sake zare ido Sadik yayi se kuma yace. “Innalillahi wa'inna ilahi rajiu'n”,Ya dubi Dije yace. “Meye sunanta ma kika ce?”. “Khausar” Dija tace. Ya maida kallonsa kan Khausar da hankalinta yabi shuke-shuken da kallo yace. “Khausar kiyi Istigfari”. Khausar kuwa kallon mamaki tayi masa kafin tace. “Saɓon Allah nayi da zanyi Istigfari?”. Habarsa ya riƙe still Fuskarsa ɗauke da Mamaki yace. “Goggo Hajjan kike cewa Masifaffiya”. Baki ta taɓe tace. “Yo ba masifaffiyar bace daga zuwa na fa kawai takama yimin bala'i”. Kai ya jinjina kafin yace. “Toh kar ki sake wallahi in Goggo Hajja taji abinfa baze miki daɗi ba”. Cikin sanyin murya Dije tace. “Allah de ya kyauta anma wannan baƙunta ai akwai kallo aciki”. Ba wanda ya sake magana har suka fito daga cikin Rafin. Gani tayi Sadik ya ɗauki wani babban kwando da sunyi ta fiya kaɗan sai ratsa cikin ciyawa ya buɗe ya ɗibi ƙwan Zabbi ya saka acikin kwando. “Me kakeyi haka?”. Khausar ta tambayesa tana kallon wajen da ciyayi masu kyau da tsari suka lulluɓe wajen. Murmushi yayi yace. “Ƙwan Zabbi nake tattarawa”. Cikin lumshe ido tace. “Ohhhh lalle kam Masha Allah abamu naci”. Murmushi yayi tare da faɗin. “Toh babu damuwa”. Haka suka riƙa tafiya suna hira jefi-jefi sun kusa fita daga cikin Rafin ne Khausar ta jiyo hayaniya na tashi kamar kasuwa anata surutu da dariya jujjuya wa tashiga yi amma bata ga inda sautin surutun ke tashi ba.Ta dubi Sadik da Dije tace. “mene nake tajin hayaniya da surutun nan kam a cikin daji?”. Sadik ne yace. “Mutanen Bishiyar ƙare zancen kane”. Da sauri ta sake duban sa tare da cewa. “Bishiyar ƙare zancen ka?,Wai mene ma'anar Bishiyar ƙare zan cenka?”. Dije ce tace. “Ai mu garin nan bamu da service, Service ɗinmu waje ɗaya ne inde mutum yana so yaje yayi waya seya je ya hau bishiyar ƙare zencen ka anan ne ake samun network idan kina wajen zaki iya kira sannan za'a iya kiranki kina sauƙa daga bishiyar ko kuma kina Matsawa daga wajen bishiyar toh shikenan Service ya yanke ba zaki samu kiyi magana ba kuma shima sai in layin MTN ne ko Zain”. Cike da Mamaki Khausar tace. “Ikon Allah wannan wani irin ruga ne?. Dama ashe har yanzu akwai irin wuraren nan daya rage aduniya?”. Murmushi Dije tayi tace. “Sosai ma”. Ahankali Khausar ta ɗaga kanta nan ta hango manyan tsaunika da bishiyoyi Kallonta ta mayar kan Dije tace. “Haba ko wannan manyan tsaunuka da bishiyoyin ai sa tare muku service da network”. Kai Dije ta gyaɗa tace. “Lalle kam da alama shi ya tare”. Ta dubi Sadik dake tsintar ƙwai tace. “Muje inga wajen”. Kai ya gyaɗa sannan yashiga gaba ita da Dije na biye dashi ta cikin wata siririyar hanya Sadik na cigaba da tsintar ƙwo'yin suna fita asirin hanyar Khausar ta hango wani ƙaton bishiyar ɗaurawa dake ɗauke da rassan bishiya masu taren yawa saura daga sama saura kuma sun zuba yayin da ƙasansa bishiyar duwatsu ne baƙaƙe masu sheƙi ke zube wanda suke kamar kujeru. Juyawa tayi ta maida Idanunta kan dandazon mutanen dake wajen mafi yawa Matasane sai kuma Dattijai tana ɗaga kanta sama ta hango Baffa Jauro yana waya. Dariya ta ƙyalƙyale dashi tace. “Baka tsoron ka faɗo ko tsohon nan?". Dije ce ta ɗan bigi ƙeyarta tare da yi mata hararan wasa tace. “Baban nawa ne tsoho?”. Murmushi Khausar tayi tace. “Toh baya tsoro ne kiga ya hau kan bishiya ya ɗane kamar birin can”. Tsayuwa Dije ta gyara tare da mata hararar wasa tace. “Ai shikam dole seya zo nan yayi waya tunda shine Jauron garin nan akwai ɓuƙatar magana da Jauro da sauran Jaurorin garirruwa”. Khausar kuwa kai ta gyaɗa tace. “Ikon Allah lalle de kam irin wannan gari haka”. Tayi maganar tana kallon matasan dake sanye da kayan Fulani kowa na amsa wayar, Idanunta ne suka sauƙa akan wata tsohuwa dake waya. Ta maida kallonta kan Dije tace. “Wannan kuma fa?”. Dije tace. “Tafff!, Wannan ƙawar Hajja Nana ce”. Kallonta Khausar ta sake yi tace. “Ƙawar Masifa de zaki ce”. Sadik dake gyara kwandon ƙwai yace. “Ki bari fa”. Ta kallesa da manyan Idanunta dake lumshe tace. “Ai da gskene Hajja Nana in ba masifa ba meta iya!?”. Duk mutanen wajen juyawa sukayi tare da zuba mata idanu jin tana kiran Hajja Nana Masifa,Wasu daga cikin mutanen ne suka ce Dije ina kika samu wannan yarinyar. Dije kuwa tayi murmushi tace. “ 'Yar Baffa Usmanu ne”. Jin Abinda Dije tace yasa sauran mutane dake saman bishiyar kashe wayansu suka sauƙo. Wani kyakkyawan Matashi fari ne ya nufosu kallo ɗaya zaka masa kasan akwai wayewa atare dashi yace. “Wannan itace 'yar Baffa Usmanu itace ƙanwar Nenne ko Masha Allah?”. Kai Dije ta gyaɗa tare da nunawa Khausar matashin tace. “Kinga wannan?”. Kai Khausar ta gyaɗa. Dije tace. “Yaron Baffa Liman ne acikin Birni yake karatun sa”. Murmushi Khausar tayi tace. “Ayyah Allah Sarki yayi kyau". Ya dubi Khausar da murmushi afuskarsa yace. “Hi Sister how are you?”. Ta mayar masa da martanin Murmushin tace. “Am fine how's everyone?”. “Fine Long time?". “Thank God”. Dije ta wani ɓata fuska Idanunta akan Khausar tace. “Kuyi magana da yaren da zanji”. Murmushi Khausar tayi tace. “Ba wani magana muka yiba kawai gaisawa ne fa”. “Toh”. Dije tace sai kuma ta maida kallonta kan Matashin saurayin tace. “Ayyah Yaya Abba nima ka koya min turancin”. Murmushi yayi yace. “Ba matsala zan koya miki Kinga ga wata ma zata koya miki”. Hira suka cigaba dayi yayin da Sadik ya cigaba da tsintar ƙwoyaye wasu ma da yawa nata tsintar ƙwoyin ko wannensu da alama akwai inda ƙwan Zabbinsa ke tsayawa akwai waya da ake sakawa atsakanin waje-jen... Baffa Jauro daya gama waya ya sauƙo tare da zuwa inda Khausar take ya riƙe hannunta suka fara tafiya sai kuma ya fara matsa hannun, Janye hannun tayi tace. “Wallahi tsohon nan ka iya mugunta inka riƙe hannun mutum kaita matsewa da faratu ni banaso”. Murmushi Baffa Jauro yayi tare da sake matse hannun!. Ashagwaɓe tace. “Wayyo na tuba ka sake”. Sake mata hannun yayi yana dariya yace. “Ohhh in dai baki daina yiwa Adda Nana rashin jiba, toh fa hakan zanyi ta matse mata ke, ga jiki ba ƙwari ba'ason wahala”. Sai kuma ya juya ya dubi Dije yace. “Dije”. “Na'am Baba”. Yace. “Kishirya Gobe idan Allah ya kaimu da sassafe zaki ɗauke ta kuje kuyi tsar Nono tare”. Kai Dije ta gyaɗa kana tace. “Insha Allah zan ɗauke ta muje tare”. Kallonsa Khausar tayi still hannunta na cikin nasa tace. “Nide inda wuya bazan yiba”. Dije tace. “Ba wuya ai zamu baki man shanu ki shafawa yatsunki yanda zai yi santsi. Kai ta gyaɗa tace. “Toh shikenan ba damuwa zanje”. Kallon Dije Sadik yayi tare da bata kwandon Ƙwan Zabbin yace. “Ki tafi dashi". Sannan ya juya ya cigaba da tafiya. “Khausar kuwa murya ta ɗan ɗaga tace. “Kaifa baza ka bimu bane”. Girgiza Kai yayi yace. “A'a ban ƙarasa ɗiba ba”. Kai ta gyaɗa tace. “Toh inde kazo ka kawo min nawa”. “Toh”,Yace sannan suka juya suka tafi. Suna shiga rugar suka nufi hanyar gidan Hajja Nana kasancewar duk gidan da zaka je seka wuce ta ƙofanta,sannan duk lokacin da taji motsi seta tambaya waye. Sallama Dija tayi cikin ladani kana suka shiga, Hajja Nana dake cikin uwar ɗaka tace. “Waye”. Cike da ladabi Dije tace. “Dije ce". Haɓa Khausar ta riƙe tare da cewa. “Ikon Allah duk mai wucewa saita tambayesa waye sai kace wata Traffick light?”. Ƙasa da murya Dije tayi tace. “Aaa ki bari Khausar kiyi ahankali kar taji”. Khausar kuwa baki ta taɓe tace. “Ai wannan abu yayi yawa wannan mulkin mallaka haka ake yi muku agarin nan”. Daga ciki Hajja Nana tace. “Dije keda waye naji kamar ana magana ƙasa-ƙasa?”. Dije tace. “Nida Khausar ce zamuje gida kai saƙo ne ƙwoyi muka kawo”. Ita kuwa Hajja Nana cewa tayi. “Toh shikenan”. Ajiyar zuciya Dije ta sauƙe sannan suka fice. Lokacin da suka fita makiyaya sun fara dawowa daga kiwo sannan sanyin magriba na sake sauƙa sanyin ya fara yawa ahaka suka isa gidansu Dije Khausar sai lumahe ido take. Suna isa suka ajiye Ƙwoyin. Dije na ƙoƙarin shiga ɗaki Khausar da Idanunta suka sake lumshewa tace. “Dije muje ki rakani ɗaukan Sweater na sanyi nake ji sosai”. Kai Dije ta gyaɗa sannan suka fice kallon garin Khausar tayi ko ina baƙi ba alamar hasken wutar lantarki ta dubi Khausar tace. “Wai kam garin nan baku da wuta ne?,tun da nazo banga ƙyallin wuta ko sau ɗaya ba?”. Kai Khausar ta gyaɗa tace. “Eh babu amma ana tada Generator”. Khausar kuwa hankalin tane ya tashi jin babu wuta garin!. Ganin yanda tayi yasa Dije sakin murmushi tace. “Kada ki damu kinga Yaya Abba shike tada Generator sannan yake sa kawa mutane Caji kuma aƙofar gidan Hajja Generator yake akwai ɗan haske kaɗan koda ba farin wata, bare kuma in akwai farin wata rana zakiga garin”. Sai asannan Khausar ta ɗan saki ajiyar zuciya dan Allah ya sani tana tsoron duhu. Bakinsu ɗauke da sallama suka shiga gidan shigarsu yayi dai-dai da kiran Sallar Magriba da akayi. A tsakar gida suka samu Hajja Nana na alwala, kallonsu tayi tace. “Kuzo kuyi alwala kuyi Sallah”. Kallon ta Khausar tayi tace. “Ni gaskiya sanyi nake ji yanzu ma rigar sanyi na nazo ɗauko kuma asamar min ruwan zafi dashi zanyi alwala”. Harara Hajja Nana ta watsa mata kafin tace. “Wa zai samar miki ruwan zafi?,Kina yarinya ƙarama yau har wani sanyi kirki akeyi! da har zaki nemi ruwan zafi”. Bakinta ta tura amma ba tace komaiba. Dije ce tace. “Muje gidanmu akwai ruwan zafi sai kiyi acan”. Kai Khausar ta gyaɗa da faɗin. “Toh shikenan” Sannan tashiga ɗakin Hajja Nana kasancewar akwai hasken lanta da aka kunna inda trolley ta yake ta nufa ta buɗe tare da ɗaukar Sweater ta sannan ta rufe trolley juyawar da za tayi Idanunta suka sauƙa akan kuliya (Mage) dake kwance akan ɗaya daga cikin gadon Hajja Nana kasancewar gado biyu ne aɗakin sai kuma ɗan shirge-shigen ta na Tsoffin ruga. Cikin matsananci tashin hankali da ruɗu mara misaltuwa daya bayyana afuskarta take faɗin. “Innalillahi wa'inna ilahi rajiu'n!!,Hasbunallahu!!!, wani'imal wakin Astagfirullah wa'atubu ilaik!!!”. Aruɗe Dije ta shiga ɗakin tana cewa. “Lafiya Khausar meye faru?”. Aruɗe Khausar ke yarfe hannunta takamar wacce ta ƙone duk jikinta na rawa takasa furta komai numfashinta na wani irin fusga na tsananin tsoro da tashin hankali, da ƙyar ta iya furta. “Kuliya”. Sai asannan Dije ta lura da kuliyar da har zuwa lokacin ke kwance akan gadon Hajja Nana. Ita kuwa Hajja Nana wani dogon numfashi taja. Dan da kusan mutuwar zaune tayi dan jin irin karajin da Khausar ɗin tayi. Ita kuwa Dija hannu tasa tashiga koran kuliyar. Daga can waje Hajja Nana ke cewa. “Kuliyar take wa wannan Ihun? zata kasheni tun kwanana bai ƙareba”. Ina ita kam Khausar bata san sunayi ba, har zuwa yanzu tsalle takeyi a tsakiyar ɗakin tana yarfa hannunta tare da furta duk addu'ar da tazo bakin, istagfari takeyi ba ƙaƙƙautawa. A gigice Dije ta fitar da kuliyar tana mai cewa. “Khausar ki nitsu ya fita, na koreshi, kuliyar Goggo Hajja cefa. Cikin tsananin tsoro da rawar jiki cike da gigita, Ta fito cikin ɗakin Hajja Nana ta nufi gidan Baffa Jauro tana cigaba da faɗin. “Innalillahi wa'inna ilahi rajiu'n Ya Allah na tuba ka yafe min”. Yayin da gaba ɗaya ilahirin jikinta ke rawa na tsananin tsoratan da tayi. Jin shiganta Aruɗe yasa Goggo Nanne fitowa daga ɗaki wato Mahaifiyar Dije. Matsawa kusa da Khausar tayi ta riƙe Hannunta tace. “Lafiya”. Asanyaye Dije tace. “Kuliya take tsoro taga kuliyar Goggo Hajjs ce take haka”. Cike da tausayinta Goggo Nanne tace. “Ayyah Subhanallah ki kwantar da hankalinki nan babu kuliya kar ki damu Khausar ki kwantar da hankalinki ki nutsu kinji?”. Kasa furta komai Khausar tayi sai Innalillahi wa'inna ilahi rajiu'n da take yi aƙasan ranta. Addu'a Goggo Nanne tashiga tofa mata kafin ta samu hankalinta ya dawo jikinta. Jauro daya fito daga banɗaki yana alwala yace. “Yau kuliya ce haka kamar wanda taga kura haka?”. Ya faɗa yana kallon yanda tsananin razana ya bayyana afuskarta. Juyawa yayi yana kallon Goggo Nanne yace. “Lalle wannan baƙunta akwai saɓani a cikinsa. Ita Addah Hajja ba zata iya rayuwa babu kuliya ba ita kuma wannan ga tsoron kuliya”. Tana sakin ajiyar zuciya tace. “Nide bazan sake shiga ɗakinta ba shegen ɗaki ga tarukuce ga duhu sannan ga kuliya wannan ɗakin har macizai za asamu acikinsa bazan sake shiga ɗakinta ba”. Murmushi Goggo Nanne tayi tace. “Ki kwantar da hankalinki kada ki damu tashi kiyi alwala ga ruwan zafi abuta”. Batace komai ba ta miƙe ta ɗauki butar ta zaga bayi sannan ta fito tayi alwala ɗakin Goggo Nanne suka shiga da Dije cikin ɗakin duhu. Araunane Khausar tace. “Daƙin duhu ni gani nake ma ko ina akwai kuliya”. Dafa kafaɗar ta Dije tayi tace. “ki kwantar da hankalinki nan babu kuliya”. Ta ƙare mgnar tana kunna lantansu mai ɗan karen haske, Kai kawai ta jinjina tare da sauƙe ajiyar zuciya ganin hasken, sannan ta tada sallah suka idar da Sallah maghariba Khausar kuwa jingina bayanta da jikin bango tayi ta fara addu'a. Dije kuwa miƙewa tayi zata fita, Kallon ta Khausar tayi tace. “Ina kuma zaki je?”. Juyawa Dije tayi ta fuskance ta tace. “Zanje in dafa mana ƙwoyin da kika ce kina so ne”. “A'a kibari ba da fawa zamuyi ba soyawa zamuyi ina akwai attaruhu da albasa da kuma maggi?”. Kai Dije ta gyaɗa tace. “Eh akwai”. “Ok to kibari sai munyi Azkhar”. “Toh”,Dije tace.Sannan ta dawo ta zauna suka cigaba da yin Azkhar ɗin Khausar nayi da ƙarfi Dije na binta wani ta iya wani kuma bata iya ba sai Khausar ta tsaya ta gyara mata suna zaune har akira Isha'i suka Idar... GEMBILA Anutse Momy ta gama shirin baccinta bayan tayi addu'a sai kuma ta lumshe Idanunta ahankali ta sake buɗesu ta juya kwanciyar ta daga hagu zuwa dama sai kuma ta tashi ta zauna baki ɗaya kewan Khausar ɗin ta ke damunta acikin yini ɗaya da bata kusa da ita se taji kamar wata tayi ba tare da ita ba gashi basu da network bare ta kira taji muryanta. Jin ƙaran Knowking ɗin ƙofa yasa Momy gyara zamanta kana ta bada izinin shiga,Anutse Haiydar ya shigo bakinsa ɗauke da Sallama kana ya zauna kusa da Momy. Murmushi Mommy tayi tace. “Haiydar lafiya ko kana bukatar wani abu?”. Kai ya girgiza yace. “Momy wallahi yau gidan nan ba daɗi da Addah Khausi bata nan”. Murmushi Momy tayi cike da ƙaunar 'ya'yan nata da kuma yanda suke nunawa juna kulawa tace. “Yau kuma?,Ko da yake dama haka kuke bakwa shiri sannan bakwa san rabuwa da juna”. Fuska ya Marerece kafin yace. “Allah yau gidan babu daɗi yau tunda gari Ya waye babu wanda yace min Haiydar kar kayi kaza, Haiydar zo in aikeka, Haiydar bakaji, Haiydar karenani, Haiydar kada fa kaci komai wurinsu Umma, Haiydar ban girme ka bane kam wai da in na saka abu bazakayi ba, Yau duk babu wanda ya faɗa min haka nayi missing ɗinta! Sosai wlh Momy Ina son Adda Khausi”. Murmushi mai cike da shauƙi Momy tayi tare da zuba musu ido. Raudat da shigowarta kenan ta Shagwaɓe fuska tace. “Wallahi nima nayi kewarta Mommy yaukam tare zamu kwana ko?”. Janyo hannunta Momy tayi tace. “Autanah ba dole ba yau In kwana dake tunda Addah Khausar bata nan”. Haiydar ne ya sake kallon Momy cikin yanayin kewar 'yar uwarsa yace. “Momy dan Allah ki kira kice ta dawo munyi missing ɗin ta”. Ramadan da Raudat suma sukayi saurin cewa. “Please Momy ki kira”. Kai Momy ta girgiza tace. “Basu da network sai dai idan sunje wajen bishiyar ƙare magarka sun kira”. Ramadan yace. “Toh yanzu Mommy Gobe wa zai Miki shara?,da wanke-wanke da kuma gyaran falo?”. Murmushi Momy tayi tana shafa kansa tace. “Zanyi ƙoƙari nayi da kaina”. Zare Ido Ramadan yayi yace. “To wallahi Momy aɗauko Miki Addah Khausi yafi Miki gidan babu daɗi idan bata nan”. Murmushi tayi tace. “Toh”,Da haka hiran yazo ƙarshe Haiydar ya miƙe kana ya ɗauki Ramadan suka tafi ɗakinsu wanda zai ka fita falon Momy ƙofar nasu na jere da ƙofar falonta, ita kuma Raudat gadon ta hau ta kwanta gefen Momyn. Acan ɓangaren su Moddibo kuwa. Zaune yake Atsarerren falonsa da yagaji da tsaruwa kana yana fitar da sihirtaccen ƙamshi mai masifar daɗin shaƙa. Yayin da M Jameel ke kwance akan 3sitter da waya maƙale akunnensa, Anutse Moddibo ya juya ya zuba masa Idanunsa tare tsarasa da su, still wayan yake Amsawa ɗauke kansa yayi ya cigaba da operating system ɗin sa kana ahankali ya sake maida Kallonsa kan M Jameel still wayar ne maƙale akunnensa. Cikin ga jiyawa da wayar da yake yi Moddibo ya zuba masa idanunsa tare da motsa laɓɓansa da suka sake yin pinch kana suka tattare saboda tsananin sanyi da akeyi yace. “Wai kai da wa kake yin wayar?”. Gyaɗa masa kai M Jameel yayi tare da juya hannunsa alamar ya kusa gamawa. Ganin haka yasa Moddibo maida hankalinsa kan system ɗin sa yana cigaba da duba muhimman saƙonnin da suke shigo masa. Wayarsa dake gefen Centre table ne yayi ƙara hannu yasa ya ɗaga nan yaga sunan Abba na yawo a screen ɗin wato Abban M Jameel. Cikin han zari yayi picking call ɗin kana yace. “Assalamu alaikum Abba Barka da dare”. Daga ɓangaren Abba yace. “Barka dai Moddibo ya gida ya kuma ɗalibai?”. “Lafiya lau Alhamdulillah Abba”. “Masha Allah kana tare da Hassan ɗinna ka ne?”. Murmushi Moddibo yayi wanda ke sake fitar da ainihin kyawun fuskarsa yace. “Eh Abba muna tare waya yake tun ɗazu nayi zaton ma da kai yake yin wayar”. Abba yace. “Aina kira wayarsa naji Line busy shiyasa nace bari na kira ka naga dare yayi bai dawo ba za'a rufe ƙofar gida”. Murmushi Moddibo yayi yace. “Ayyah Abba yau kam abarshi mu kwana tare gashi naga alamun Agajiye yake bacci ma yake ji”. Kai Abba ya gyaɗa yace. “Toh shikenan Moddibo ayi bacci lafiya Allah ya tashe mu lafiya amma gobe da safe kuzo ina son ganin ku”. Kai Moddibo ya gyaɗa cike da mutuntaka yace. “Toh insha Allah Abbah”. Kana ya katse kiran. kallon M Jameel yayi sai kuma ya ajiye System dake kan ƙafarsa ya miƙe ya isa inda M Jameel yake yasa hannu ya cire wayar daga kunnensa ya duba screen ɗin sai yaga number ba suna saidai aƙasan Number ansa Bahrain wato ƙasan Bahrain. Kallon M Jameel yayi yace. “Ooo kaida Jalaludeen ne dama?”. Kai M Jameel ya gyaɗa yace. “Eh shi ya hana ince da kai dashi nake waya”. Murmushi M Jameel yayi yace. “Yayi kyau”. Jalaludeen abokinsa ne tare sukayi karatu a Jami'atul Madina asalin Balarabe Bahrain ne... Ajiyar zuciya Moddibo ya sauƙe yace. “Abba ya kira yace baka koma ba har dare yayi sai nace zamu kwana tare yace gobe yana son ganinmu”. Kai M Jameel ya gyaɗa da faɗin. “Allah ya kaimu”. “Ameen”. Moddibo ya amsa tare da kallon M Jameel yace. Bacci na keji zanje nayi wanka”. Zare Ido M Jameel yayi yana kallon Moddibo yace. “Wallahi inba cikin kashi na faɗa yanzu ba ba zanyi wanka ba yanda ake tsuga wannan sanyi agarin nan. Kai Moddibo ya girgiza ba tare da yace komai ba ya wuce Bedroom. wanka yayi da ruwa mai ɗumi, kana yayi shirin bacci. Washe gari, da safe bayan sun dawo daga masallaci sashen Innayi suka nufa lokacin da suka shiga tana zaune kan darduma tana lazimi M Jameel ya zauna kusa da ita tare da riƙo tafin hannunta yace. “Barka da safiya tsohuwa mai ran ƙarfe!”. Murmushin fuskarta ta faɗaɗa tare da damƙe hannunsa dake cikin nata tace. “Jameel Ubangiji Allah ya Albarkanci rayuwarku”. Ya amsa da. ”Ameen Innayi”. Shi kuwa Moddibo kusa da ita ya matsa ya ɗaura kansa akafaɗarta yana mai lumshe idanunsa ahankali yace. “Barka da safiya Innayi”. Hannunta tasa ta shafa fuskarsa tare da cewa. “Fatan ka tashi lafiya ya ƙoƙari?”. Ya amsa da. “Alhamdulillah” sai kuma ya miƙe tare da kallon M Jameel da still hannunsa ke cikin na Innayi yace. “Mu je ko”. Bai jira cewarsa ba ya fice daga sashen nata kana ya nufi nasa yana shiga kai tsaye Bedroom ya wuce ya cire naɗin Hiramin dake wuyan sa da kuma jallabiyar. Kai ya shiga bathroom Masha Allah Komai na cikin toilet wanka ya fesa kana ya fito bakinsa ɗauke da addu'a “Gufra naka”.Alokacin daya ziro ƙafarsa ta dama zuwa cikin Bedroom ɗin ya fito M Jameel kuwa jin ƙamshin sabulun wankan da kuma tularensa yasa ya ɗago kai sai kuma ya miƙe ya shiga toilet ɗin. Shi kuwa Moddibo zama yayi agaban dressing mirrow ya shafa mayukan sa tare da taje yalwataccen sumarsa kana ya miƙe ya buɗe durowarsa Masha Allah kayane aciki masu uban yawa fannin jallabiya da ban fannin yaduka da ban haka zalika fannin ƙananun kaya daban duk da cewa bai fiye amfani dasu ba yana tsaye awajen har M Jameel ya fito daga wanka bai ɗauki komai ba. Murmushi m Jameel yayi tare da nufar jikin durowar yana cewa. “Nasan koda zaka kwana nan ba zaka taɓa cire kayan da zamu sanya ba kai de inba jallabiya ba baka ganewa ko wani irin kaya”. Moddibo kuwa murmushi yayi Aransa yana jinjinawa M Jameel yanda yake iya fahimtar komai nasa koda kuwa ƙwaƙa-ƙwaran motsi yayi yasan me yake nufi... M Jameel kuwa Wani boyel Sky blue mai gidan dara-dara ya ciro musu tare da boxer da kuma singlet Fari ƙal. Kallon Moddibo yayi tare da miƙa masa. Murmushi Moddibo yayi tare da karɓa yana kallon kayan amma bai ce komai ba sai ya juya ya kimtsa. Masha Allah wani irin kyau na musamman Moddibo yayi acikin kayan kalar shigar sai ta kasance tamkar kalar sararin samaniya ƙirjinsa na ƙiran jarumtaka ya bayyana acikin rigar kana yalwataccen sumar kansa ya kwanta luf yana sheƙi,Anutse ya juya wajen M Jameel dake miƙo masa takalmi da hula kalar sky blue Masha Allah m Jameel ma sosai Yayi kyau acikin kayan sai suka kasance tamkar tagwaye masu tsananin ƙaunar junansu. Atare suka fice sashen Innayi suka nufa tun daga farfajiyar tsakar gidan Moddibo ya lumshe idanunsa yana jinjinawa tsaftar Kakar tasa har sanda suka isa ƙofanta inda sanyayyan ƙamshi turaren wuta ke tashi. Ganinsu atare yasa ta sakar musu da murmushi atare suka shiga ɗakin suka zauna. Ta dubesu cikin ƙaunarsu tace. “Ubangiji Allah ya Albarkanci rayuwar ku Allah yasanya farin ciki acikin rayuwarku Ubangiji ya tsareku da dukkan sharrin mai sharri”. Cikin jin daɗin addu'ar da take musu ako yaushe suka amsa da. “Ameen Innayi”. Innayi kuwa miƙewa tayi ta haɗo musu tea mai zafin gaske saboda sanyin da akeyi sosai amsa sukayi. A hankali Modibbo ya ɗan zuƙan tea ɗin ahankali har ya Ida shanyewa zuwa lokacin tuni M Jameel ya shanye nasa. Yana ƙoƙarin ajiye Mug ɗin yaga M Jameel ya tsaresa da ido Harara Moddibo ya watsa masa shikuma saiya sakar masa da murmushi. Kallon Innayi Moddibo yayi yace. “Zamu je gaida Abba”. Jinjina kai Innayi tayi tace. “Idan kunje ku gaishe min dashi”. Moddibo na miƙewa yace. “Zaiji insha Allah”. Sannan suka fice. Suna fita suka nufi inda mota ke ajiye M Jameel ne ya buɗe gefen Driver ya shiga yayin da Moddibo ya shiga mazaunin mai zaman banza ahankali M Jameel yayiwa motar key suna isa gate ɗin Moddibo ya fita ya buɗe musu gate sannan M Jameel ya cinna hancin motar yafita saida Moddibo ya sake rufe gate ɗin kafin ya koma cikin motar M Jameel ya tayar suka bar unguwar. Anutse M Jameel ya dubi Moddibo da idanunsa ke lumshe yace. “Anma aikin makarantar nan zai yi kyau domin masu aikin sun san makamar aikinsu”. Shi kuwa Moddibo kai ya gyaɗa da faɗin. “Sosai Insha Allah”. Tafiyar Mintuna Kaɗan sukayi suka isa gidansu M Jameel Hon yayi mai gadin ya taho da sauri ya buɗe musu tamfatsetsen gate din. Wow Masha Allah babban gida ne wanda yake ɗauke da Sashe huɗu sai kuma BQ da kuma wajen ajiye motoci kamar takwas zuwa goma sai ɗakin mai gadi cikin gidan akwai shuke-shuke saida basu da yawa sosai bayan sunyi parking sun fito ajere suke cikin tafiyar nutsuwarsu da tazame musu jiki kai tsaye sashen mahaifin M Jameel ya nufa dasu. Adai-dai ƙofar da zai sa dasu da falon Mahaifin M Jameel suka haɗu da Hajiya Karima kallon Jameel tayi kana ta kawar da kanta wani irin tsuke fuska tayi ganin Moddibo abayan M Jameel. Cike da ladabi M Jameel yace. “Ina kwana Aunty Karima”. Fuska ta sake tace. “Lafiya lau ɗana ya gida ya kuma ƙoƙari??”. “Alhsmsulillah ya amsa”. Yana mai shafa sajensa Shi kuwa Moddibo cikin tsuke fuska alamun ba wargi ataƙaice yace. “Ina kwana”. Wani irin kallo ta watsa masa kafin tace. “Kaska raɓi mai jini anzo kenan?”. Shiru Moddibo yayi tare da kauda kansa kamar bai jitaba. Sai ma Murmushi da yayi tare da kallon gefen dama inda Aunty Larai Amaryar Aunty Karima ke tare da ce mata. “Yau barka dai”.yayi mgnar yana mai tsare fuskarsa da ido alamun yana nazartar ta, Ita kuwa Aunty Larai cikin sakin fuska tace. “A'a to Moddibo ya kuka tsaya nan ku shigo daga ciki man Jameel”. Ta ƙare mgnar tana kallon Jameel tare da juyawa ta nufi cikin falon Daddyn Jameel din. Cikin jin yanayin ɓacin ran da kalaman Aunty Karima suka sa mishi yace. “Gamu nan shigowa Aunty Larai”. Ya kare mgnar tare da ɓata fuska cikin rashin jin daɗin abinda ta yiwa amininsa yace. “Aunty!Aunty!!, Meyesa!!?, Meyesa!!!?”. Cikin taune lips inta dubesa tace. “Jameel gaskiya ne ai, amma ba zaka gane ba, ba zaka yarda ba sabida ya fika wayo. Kawai dai ya zama dole in faɗa maka”. Shiru M Jameel yayi tare da juyawa wajen Moddibo wanda har zuwa lokacin yake tsaye hannunsa M Jameel ya riƙe yace. “Dan Allah kayi haƙuri inda sabo yaci kasaba da halin Aunty na roƙeƙa Kayi haƙuri mushiga daga ciki”. Murmushi Moddibo ya sakar masa ahankali ya furta. “Bakomai me zatayi ya dameni sam babushi tunda tana son aminina”. Yayi mgnar da iya gskyarsakan suka shiga cikin falon. Ita kuwa Aunty Karima tsaki taja tare da barin wajen tana maijin tsanar Moddibo. Zaune suka samu Alh Bashir Mafindi Shahararren mai kuɗi daya sharahara aƙasa da kuma faɗin Afirca baki ɗaya mutum mai tsananin tausayin al'umma da jin ƙai. Hannu ya buɗe musu cikin nutsuwarsu suka ƙarasa Moddibo ya nufi gefen damansa yayin da M Jameel ya nufi gefen hagunsa ya rungumesu tare da buga kafaɗar su. Cike da so yace. ‘Yan ta gwayena Ubangiji Allah ya Albarkanci rayuwar ku ina jin dadin ganinku atare kunyi kyau tamkar matasan Larabawa Allah Ubangiji ya nuna min aurenku”. Moddibo kuwa murmushi yayi shikam sai ya zo wajen Abban Jameel ake masa maganar aure sai yaji abin banbara ƙwai duk da yasa ba duk lokacin da yazo wajen Abba saiya masa Maganar amman kullum a baƙuwa yake jin kalmar a cikin kunnuwansa. Cike da ladabi da kuma girmamawa suka gaishesa cike da ƙaunarsu ya amsa da. “Lafiya”. Kana ya tambaye su ya ɗalibai?. Suka haɗa baki wajen faɗin. “Lafiya lau Alhamdulillih”. Zama Abba yayi bisa kujera. Kana su kuma suka zauna a ƙasa bisa tattausan carpet ɗin, cikin kula Abba ya ɗan sunkuyo ya kalli M Jameel kana yace. “Yanzu kaga damuna ta kusa sauƙo za'a fara shuke-shuke to inason bana zan shuka Auduga mai yawa saboda ina son zan habaƙa Company dake Marrocco muna buƙatar Auduga mai yawa domin mun samu haɗin guwar da wani ɗan Saudia wurin sufurin Sallayoyi da zannuwan gadaje da kuma Abayoyin na mata”. Kai M Jameel ya gyaɗa tare da cewa. “Eh Abba hakan yayi Allah ya sanya alkhairi”. Shima Moddibo yayi Murmushi da faɗin. “Allah yabada sa'a”. Cikin jin dadi Abban yace. “Ameen. Yauwa sai kuma noma shinkafa da zamuyi mai yawa da alkama, dan Company kayan masarufin dake Ɓadamaya yana buƙatar ninkin abinda yake sarrafa a shekara, domin samun haɗin guiwa da shi'ar ƙasar Niger”. Kai suka jinjina alamun gamsuwa kana cikin kula Abban yace. “Na sani kuma na fahimta, cewa akan su Asma'u ne ka nacewa karantarwa da kai da amininka. To Alhamdulillah na baku dama, amman ku sani suna gama secondary School, dole ku bar karantar wannan Moddibo ina buƙar taimakonku a Company's ɗin tunda Allah yayi kun karanci Business ɗin nan kafin ma ku tafi Jami'atul Madina. Babana yanzu girma ya cinmini abubuwa sunayi min yawa dole ina bukatar tai makonku”. Ya kare mgnar yana dafa kaɗan Jameel. Cikin sanyi Jameel ya ɗago kansa ya kalli mahaifin nasa kana cikin sashi farin ciki yace. “Allah ya kaimu lokacin Daddy in Sha Allah zanyi maka dukkan abinda kake so, muddin ina raye”. Cikin jin dadi yace. “Kaifa Moddibo baƙace komai ba?”. Murmushi gefen baki yayi tare da cewa. “Daddy duk inda J yake to in sha Allah ina nan”. Cike da jin daɗin Alh Bashir Mafindi ya shafa kansu tare da cewa. “Allah yayi muku al'barka". Cike da jin daɗin sukace. “Amin Ya Allah Allah ya ƙara nisan kwana da lfy”. “Amin Ya Allah”. Abba ya amsa tare da nuna musu dinning area da hannunsa, inda Aunty Larai ke shirya dinning ɗin tama mai murmushin jin tattaunawarsu. Sai kuma ya kalli Moddibo kana yace. “Bismillah kuje kuyi Breakfast”. Moddibo kuwa kai ya girgiza a hankali yace. “Daddy na ƙoshi”. Kallonsa Daddy yayi cikin kulawa yace. “Meyesa haka ne Moddibo gsky ni bana son yadda kake in kazo gidan nan kaci abinci sai kaƙi ci”. M Jameel ne ya amshi zancen da cewa. “Rabu dashi Daddy in baici ba sai muyi masa ɗure”. Murmushi Daddg yayi tare da faɗin. “Aikam". Moddibo kuwa harara ya wurgawa M Jameel. Adam ƙanin M Jameel yaron Aunty Karima ne yashigo ganin M Jameel yasa ya faɗaɗa Murmushin sa yace. “Yaya Jameel Ina kwana?”. Cikin murmushi M Jameel ya mayar masa da. “Lafiya lai alhamdulillah Adam ya school”. Adam kuwa kallon tsana ya watsawa Moddibo ba tare daya gaishe saba dan gani suke yana amfani da M Jameel ne wajen cin dukiyar mahaifinsu ko kaɗan M Jameel baiji daɗin abinda Adam yayi wa Moddibo ba, haka yasa ya haɗawa yaron fuska. Acan Rugar Jauro yaya kuwa Washe gari. Bayan Khausar sunyi Sallar asbah tare da Azkharul sabah ɗakin Goggo Nanne suka shiga ita da Dije suka gaisheta, Ta amsa fuska asake Idanunta akan Khausar tace. “Ya kwanar baƙunta da kuma tsoron kuliya?”. Murmushi Khausar tayi tana wasa da yatsun hannunta har yanzu Atsorace take idan akwai abinda tafi tsoro acikin dabbobin duniya to kuliya ce da ƙadaggare. Dije ce ta miƙe tace. “Mun tafi gidan Hajja Nana”. “Toh adawo lafiya". Miƙewa sukayi suka fita ahanya Khausar ta dubi Dije cikin sanyin murya tace. “Idan munje Kar mu daɗe tsoron gidan nake". Kai Dije ta gyaɗa suka cigaba da tafiya bakinsu ɗauke da Sallama suka shiga Hajja Nana dake hakimce akan kujeranta ta amsa Khausar kuwa kusa da ƙafafun Hajja Nana ta zauna tace. “Ina kwana Hajja Nana”. Ta dubeta fuska asake ta amsa tana jin ƙaunar ta aranta. Dije ma gaisheta tayi ta amsa fuska asake. Miƙewa Khausar tayi tace. “Mu tafi”. Kallonta Hajja Nana tayi tace. “Ki zauna mutanen garin zasu zo gaisheni zan gabatar dasu awajenki”. Khausar kuwa narai-narai da idanu tayi har cikin ranta take tsoron gidan Hajja Nana Allah ya sani tana masifar tsorob kuliya, jiki asaɓule ta zauna tare da riƙe Dije suka zauna tare. Suna zaune Baffa Jauro yazo cike da girmamawa da kuma ladabi yace. “Addah Hajja ina kwana”. “Lafiya ta amsa”,tare da kallon Khausar dake takure tace. “wannan shine ƙanina dake bina” Murmushi Khausar tayi tare da gyaɗa kai tace. “Baffa ina kwana”. Dariya yayi yace. “Lafiya Audiii ya fargaban kuliya!?”. Baki ta ɗan tura amma batace Komai. Can sai ga Goggo Nanne Kusa da Khausar ta zauna tace. “Addah Nana ina kwana”. Ta amsa da lafiya tare da kallon Khausar tace. “Wannan itace matar Jauro wacce kuka kwana agidanta sunanta Nanne ita ce kuma takwaran marigayi yayarki”. Kai Khausar ta gyaɗa tana sake damƙe hannun Dije dake cikin nata. Can sai ga Garga yazo idanun sa akan Khausar ya mata murmushi hannunta ya riƙe yace. “Addah Nana ina kwana ya kwanan baƙuwa?”. Hajja Nana kuwa taɓe baki tayi tace. “Ga tanan matsoraciya saboda kuliya taƙi kwana anan". Murmushi Garga yayi yace. “Audii ki zama jaruma Mahaifinki fa ba rago bane babban jarumi ne”. Murmushi tayi amma batace Komai ba. Hajja Nanan ce tace. “Wannan shine Garga shike bin Jauro. Can sai ga wata mata tazo itama ta gaida Hajja Nana. Hajja Nana ta dubeta tace. Wannan itace Dijarro matar Garga”. Cikin sanyin murya Khausar ta gaisheta, Cikin sakin fuska Dijjaro ta amsa. Ba daɗewa saiga Liman yazo sanye cikin Alkyabba kansa naɗe da hirami kusa da ƙafafun Hajja Nana ya zaune cike da ladabi da kuma dattako yace. “Addah Hajja ina kwana”. Ta amsa da. “Lafiya”.Sannan ta dubi Khausar tace. Wannan shine Aliyu Limamin garin nan Uwarmu ɗaya Ubanmu ɗaya mutum ne mai tarin Ilimin addini”. Cike da ladabi Khausar tace. “Ina kwana”. “Lafiya lau ya kwanan baƙunta?”. Ta amsa da “Alhamdulillah”. Bayan tafiyarsa sai ga matansa biyu Rabi da Loddo,Kai kawai Khausar ke gyaɗawa. Ita de Khausar ta kasa sakewa,Ahaka suka riƙa zuwa duk wanda yazo Hajja Nana zata gabatar wa da Khausar shi. Can saiga Yaya Abba yazo Hajja Nana tace. “Wannan shine Abba ɗan ƙanina ne liman shi aka tura karatu birni yana karatun arnanci irin wanda kike yi”. Abba kuwa ƙasa da kai yayi yana murmushi. Ita kuwa khausar kallon Hajja Nana tayi tace. “Wai waya ce Miki karatun Arnanci mukeyi?”. Hannu Yaya Abba ya ɗaya mata alamar tayi shiru!. Khausar kuwa ta wani juya masa manyan Idanunta tace. “Taya ba karatun Arnanci mukeyi ba tace karatun Arnanci mukeyi ko ance mata acoci muke zuwa karatun?”. Kallonta Abba yayi cikin harshen turanci yace. “Please Khausar Enough, Don't sey anything again”. Zare Ido Hajja Nana tayi tace. “Abbah zagina kayi ka juya yare zaka zageni da yaren Arna!??”. Kai Yaya Abba ya girgiza yace. “Wallahi ba zaginki nayi ba Goggo Hajja na isa in zageki?,Ai Babana ma bai isa ya zageki ba bareni”. Kai ta gyaɗa kana tace. “Oooo”. khausar kuwa murmushi tayi tace. “Hajja Nana zamu tafi!". Kai ta gyaɗa alamar toh kasancewar duk sun gama zuwa, Sai kuma ta kalli Dije tace. “Ki ɗauke ta ki zagaya da ita gidajen kowa ki gabatar da ita”. Kai Dije ta gyaɗa sannan suka miƙe suka tafi kamar yanda Hajja Nana ta faɗa haka Dije ta riƙe zagayawa da Khausar duk gida jen ƙannen Hajja Nana da kuma 'yan uwa aƙarshe suka shiga gida Umar Autansu Hajja Nana... Abakin ƙofa suka samu Baffa Umaru kallo ɗaya zaka masa kasan jarumin namiji ne mai cike da haiba da kuma ƙwarjini. Ya dubi Khausar da murmushi afuskarsa yace. “Girman biredi wayon shayi”. Murmushi tayi tace. “Ni dai ba girman biredi bace”. Yana dariya yace. “Shekaranki nawa?". Tayi murmushi da faɗin. “Sha takwas". Ya wara ido yace. “A'a, ai babanki ma da kaɗan yafi haka”. Ɓata fuska tayi tace. Meyesa kuma zaka sa Babana?banaso shi kam baya rasu ba abarshi ya huta mana”. Murmushi mai cike da ciwo yayi tare da janyo hannunta ya ajiye ta gefensa kana a yace. “Ai nima Babanki mutumi nane Shiyasa duk maganata nake kawo sunansa saboda banaso amanta dashi. Ni sa'an sane tare muka taso mukayi wasan ƙasa banaso amance shi ina so ko yaushe arika kiran sunan sa ana masa addu'a”. Khausar kuwa murmushi tayi tace. “Nagode sosai Allah ya saka da alkhairi”. “Ameen”,Ya amsa sannan ya kamata hannunta suka shiga cikin gida. Da fara'a matarsa mai suna Adama ta yi musu sannu da zuwa sannan ta shimfiɗa musu abin zama bayan sun zauna ta kawo musu ɗumamen tuwon shinkafa da miyar taushe sai kuma madaran shanu mai zafi. Kallon Umaru Khausar tayi tace. “Har matarka ta gama abinci?”. Kai ya gyaɗa ita kuma matarsa murmushi tayi kana tace. “Eh saboda shi jarumi ne baya son zama da yunwa kinsan shine garkuwan rugan nan”. Wara Ido Khausar tayi tana dariya tace. “Ba wani Garkuwa kawai de kina kurara sane”. Murmushi Adama tayi tace. “Shikenan duk lokacin da Arnan maƙota suka kawo farmaki zakisan shine garkuwan rugan nan". Murmushi sukayi Dukansu sannan ya fice Khausar da Dije suka wanke hannu suka fara cin abincin bayan sun gama ne suka tafi. Kai tsaye Ruga suka nufa suna isa Rugar aka ɗaurewa Khausar shanu sannan Dije ta shafa mata man shanu ayatsu saboda yayi santsi tsugunnawa tayi aka ɗaura mata ƙwayar ya akan cinyarta kana cikin azama ta kai tatsuniya kan bakin n......! *WOHOHO IN KAJI ANA ƘI GUDU TABBAS SA GUDU NE BEZO BA* _Ina kuke Ma'aurata masu sha'awar ganin sun zama taurari kuma fitilu a idanun mazajensu Uwar gida,Amarya,Tsakar gida,hadda tan kaɗen gida Shararriya kuma ƙasaitacciya data saba kawo muku nau'ikan sirrin sahihan magungunan ma'aurata wato *AYSHA ALIYU GARKUWA* Garkuwar Marubuta ayau ma ta dawo muku da Ingantattun magungunan mata masu kyau da inganci domin gyara kanki ki zamto tauraruwa a idanun mijinki...Muna da Ingantattun Abubuwa kamar haka_ :_Munada Garin mallaka, garin maɗi, garin Hakkin mayi, garin ɓelɗamhi Garin ilanwaddihi, Gumbar da ba'a baiwa mai kishiya, Gumbar kolli mai kellin al'khairi, Gumbar Riɗi wato 3 in 1, Gumbar makwaranyi, Masin Maliƙi mai masifar ƙarfi da matse mace, ka masin Daɗi har Maɗigan Akwai, kwanon ƙasaitacciyar mace mai masifar kyau da ratsa jiki da samar da inƙantacciyar ni'ima yanada abubuwa masu kyau haɗinsa, Zumar goron tula mai masifar kyau, tsumin dabino, mai ratsa jiki, tsumin Riɗi mai ƙarfi, Furar Mata mai tsastsafo da ni'imantaccen damshi, Cida kaza, Ciccibi Abodi, Tsumin Ɓaure, tuwon ɓauren, kana akwai maganin sanyi sadidan, da dai sauransu...Se kuma fannin ƙamshi kasance da Shu'umin ƙamshi wanda ze gigita ƙwaƙwalwar Oga tare da jin ko wacce mace bata kaiba...._ _Shin ko kina da labarin Miskilinci da ƙasaitar Rayyan Naaan amma lokaci ɗaya ya zamto zautacce sakali akan soyayyar Jannart bakomai Jannart ta riƙe ba face sirrinkan gyara da kuma shu'uman humran da kulaccar sirri na Aysha Aliyu Garkuwa(Tubali) tabbas taga tasirin haka domin Naanunta ya zame mata tamkar bawa_ _Shin ko kinsan sihirtaccen haɗin da Aysha ke sha kenan ta zamto tauraruwa a idanun Hamma Yusuf(Miwasmiti)...Tabbas Mahmud ya zamto zautacce kuma makaho akan sauyayyar Bazawara wato khadijarsa duk da kuwa gashi da budurwa(Namiji Baya Kaɗan) ko kinsan hakan nada alaƙa da amfani da sahihan maganin da kuma shu'uman humran Aysha Aliyu Garkuwa??.Nasan ba zaka ku manta da irin kima da kuma darajar da Aysha ke dashi acikin Idanun Sheik Jabeer ɗin ta duk da kuwa shekaru sunja anma jinta yake tamkar budurwa 'yar sha bakwai(Garkuwa) sirrin hakan na tare da Ingantattun kuma sahihan magungunan Aysha Aliyu Garkuwa Wato Garkuwar Marubuta da kuma Ma'aurata na tabbata kunsan da cewa basirarta ba'a iya rubutun littafi ya tsaya ba hadda inganta rayuwar ma'aurata ta hanyar kawo musu Nagartattun abubuwa Ga duk wacce ta shirya saya seta tuntuɓi number ta 09097853276 muna iya tura kayan mu aduk inda kuke afaɗin Nigeria harma da ƙetare Dan Allah 'yar uwa idan baki shirya siyaba kada kiyi min magana muɓatawa kanmu lokaci...._ 🤝🏻🤝🏻🤝🏻🤝🏻🥰😘sai.kunzo. sayan na gari maida kuɗi gida, By ' *GARKUWAR MARUBUTA* [19/07, 7:59 PM] Halimatu A/rahman Sadeeya: 📝🍇✨💫⏰🤴🏻👹❤️❤️❤️🍇 *SAKAYYAH* _Page 6_ _NA_ *AYSHA ALIYU GARKUWA* 🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 *FREE PAGE* *LITTAFIN SAKAYYAH na kuɗine, wannan Free page ne, ƴar uwa ki biya ki karanta cikin Aminci ba haƙƙin wani a kanki 1k ne kacal 0661110170 GTBank AISHA ALIYU GARKUWA. Sai ki turo min shaidar biyanki ta WHATSAPP 09097853276. *WOHOHO IN KAJI ANA ƘI GUDU TABBAS SA GUDU NE BEZO BA* _Ina kuke Ma'aurata masu sha'awar ganin sun zama taurari kuma fitilu a idanun mazajensu Uwar gida,Amarya,Tsakar gida,hadda tan kaɗen gida Shararriya kuma ƙasaitacciya data saba kawo muku nau'ikan sirrin sahihan magungunan ma'aurata wato *AYSHA ALIYU GARKUWA* Garkuwar Marubuta ayau ma ta dawo muku da Ingantattun magungunan mata masu kyau da inganci domin gyara kanki ki zamto tauraruwa a idanun mijinki...Muna da Ingantattun Abubuwa kamar haka_ :_Munada Garin mallaka, garin maɗi, garin Hakkin mayi, garin ɓelɗamhi Garin ilanwaddihi, Gumbar da ba'a baiwa mai kishiya, Gumbar kolli mai kellin al'khairi, Gumbar Riɗi wato 3 in 1, Gumbar makwaranyi, Masin Maliƙi mai masifar ƙarfi da matse mace, ka masin Daɗi har Maɗigan Akwai, kwanon ƙasaitacciyar mace mai masifar kyau da ratsa jiki da samar da inƙantacciyar ni'ima yanada abubuwa masu kyau haɗinsa, Zumar goron tula mai masifar kyau, tsumin dabino, mai ratsa jiki, tsumin Riɗi mai ƙarfi, Furar Mata mai tsastsafo da ni'imantaccen damshi, Cida kaza, Ciccibi Abodi, Tsumin Ɓaure, tuwon ɓauren, kana akwai maganin sanyi sadidan, da dai sauransu...Se kuma fannin ƙamshi kasance da Shu'umin ƙamshi wanda ze gigita ƙwaƙwalwar Oga tare da jin ko wacce mace bata kaiba...._ _Shin ko kina da labarin Miskilinci da ƙasaitar Rayyan Naaan amma lokaci ɗaya ya zamto zautacce sakali akan soyayyar Jannart bakomai Jannart ta riƙe ba face sirrinkan gyara da kuma shu'uman humran da kulaccar sirri na Aysha Aliyu Garkuwa(Tubali) tabbas taga tasirin haka domin Naanunta ya zame mata tamkar bawa_ _Shin ko kinsan sihirtaccen haɗin da Aysha ke sha kenan ta zamto tauraruwa a idanun Hamma Yusuf(Miwasmiti)...Tabbas Mahmud ya zamto zautacce kuma makaho akan sauyayyar Bazawara wato khadijarsa duk da kuwa gashi da budurwa(Namiji Baya Kaɗan) ko kinsan hakan nada alaƙa da amfani da sahihan maganin da kuma shu'uman humran Aysha Aliyu Garkuwa??.Nasan ba zaka ku manta da irin kima da kuma darajar da Aysha ke dashi acikin Idanun Sheik Jabeer ɗin ta duk da kuwa shekaru sunja anma jinta yake tamkar budurwa 'yar sha bakwai(Garkuwa) sirrin hakan na tare da Ingantattun kuma sahihan magungunan Aysha Aliyu Garkuwa Wato Garkuwar Marubuta da kuma Ma'aurata na tabbata kunsan da cewa basirarta ba'a iya rubutun littafi ya tsaya ba hadda inganta rayuwar ma'aurata ta hanyar kawo musu Nagartattun abubuwa Ga duk wacce ta shirya saya seta tuntuɓi number ta 09097853276 muna iya tura kayan mu aduk inda kuke afaɗin Nigeria harma da ƙetare Dan Allah 'yar uwa idan baki shirya siyaba kada kiyi min magana muɓatawa kanmu lokaci...._ Akwai daya bangaren wato *KAMSHI* Kimarki gyaranki da kamshinki. Matan da suka gane suka san yanda za su kankaro da mutunci su ne masu amfani da kayan gyara da kuma sanyaya jikinsu da kamshi, ina da turaren wanka da na bandaki na daki na jiki da na kaya dana tsuguno kamshin turarena na dabam ne mai sanyaya zuciyar wanda ya shaka ina da kayan kamshi na amarya da na maijego da na uwargida da dukkan macen da take kokarin mayar da kanta mai daraja a idon kowa ta zamo sarauni a idon mijinta, akwai shu'umar humra, sayan na gari maida kuɗi gida, banda karanta yayin gyara Hajia. Zaku iya samun kayyakina a duk garin da kike, zakiyi min mgn ta whatsApp number na 09097853276 domin yin zaɓinki, ko karin bayani, zaki tura kuɗin ta account na 0005388578 Jaiz bank AISHA GARKUWA ALIYU in mun gama mgna zan sa miki kaya a mota yazo duk garin da kike, in baki shirya saya yanzuba Please kada mu wahal da juna ki bari sai kin shirya kafin kiyi min mgn. 🤝🏻🥰😘 Daga taku AYSHA ALIYU GARKUWA *(GARKUWAR MA'AURATA)* Cike da mamaki Sadik ke kallon yanda take ta tsar Nonon cike da tsantsar ƙwarewa da rashin tsoro. Fuskarsa ɗauke da murmushi ya juya ya kalli Baffa Jauro kafin yace. “Ikon Allah Baffa kalli yanda take tatsan”. Murmushi Baffa Jauro yayi yace. “Ai ‘yar na gadana tafi ‘yar na koya gadonta ne fa abune da ajinin mu yake in Bata iya ba ai sai muce ba tsatson mu bace”. Ita kuwa khausar murmushi tayi ita da kanta tana mamakin yanda ta riƙe bakin Nonon shanun tana tatsa Shar-shar kawai Nono mai ɗumi yana zubowa. Ƙwayar dake cinyarta ne ya cika Dije ta janye ta sake sanya mata wani cike da shauƙi da kuma jin daɗi take cigaba da ta tsar Nonon kamar wacce tunda canma ta iya. Baffa Jauro na murmushi ya janye ƙwarya ta biyu ya sake saka mata wani yana murmushi yace. “Zan kaiwa Addah Hajja Nonon da kika tatsa da hannunki”. Murmushi kawai tayi yayin da Sadik da Dije ke cigaba da mamakin ƙwarewarta. Bayan ta tatso na ƙarshe ne Baffa Jauro yace. “Kusha toh”. Ita kuwa khausar ɗaga ƙwaryan tayi ta kai bakinta sai kuma ta cire kana ta mayar da kallonta kan Baffa Jauro tace. “Nikam bazan iya sha ba suga ba”. Murmushi Baffa Jauro yayi tare da buɗe tandu duma dake hannunsa wanda ke ɗauke da zuma ya zuba mata aciki kana yace. “Toh kusha”. Kai Khausar ta gyaɗa masa sannan takai ƙwaryar ɗanyen madaran mai ɗumi bakinta tasha sosai tana lumshe Idanunta kafin ta miƙawa Sadik yasha kana ya bawa Dije sauran. Bayan sun shanye suka ɗauko hanyar komawa gida. Khausar ta ɗaga Kaita kalli gefen damanta inda taji muryar Yaya Abba, ta hango Yaya Abba da Sule yayan Dije da take bi zaune acikin shagon caji da kuma kati wanda duk lokacin da Yaya Abba ya koma makaranta Sule ke zama ashagon kallon Sadik da Dije Khausar tayi tace. “Ayyah mu biya ta wajen Yaya Abba mu gaisa”. “Toh” Suka ce sannan suka nufi shagon kana suka gaisa. Kallon Khausar Yaya Abba yayi yace. “Khausar kisan yanda zaki zauna da Goggon mu kar kinayi mata gautsin baki ba daɗi gsky”. Khausar kuwa jin abinda Yaya Abba yace yasa ta taɓe baki kafin tace. “Ni gaba ɗaya haushin matar nan nakeji idan ita bata sani ba ita tasa na tsani zuwa Rugar nan ba abinda yake ban haushi da Rugar nan kamar rashin wuta,Jiya duhu kamar zai kashe mutane sannan gashi ta ajiye Kuliya aɗakinta baki ɗaya garin ba daɗi wallahi”. Ta ƙarashe tana mai ya mutse fuska. Murmushi Abba yayi yace. “Shine kenan matsalar duhu na damunki!?”. Kai ta gyaɗa masa kai da faɗin. “Eh”. Yace. “Shikenan toh za'a haɗa wutan Gen.ɗin nan dana ɗakinta shikenan ko?, Saboda kar kuna samun matsala atsakaninku bakisan yanda take son Babanki ba kema kullum zakiji tana maganarki amma ta shedeki cewa kina da gautsin baki ke ba irin Nanne data raina bace kinga su suna mata biyayya duk abinda take so”. Kallon sa Khausar tayi kafin tace. “Toh sude sunga zasu iya ne wannan ai mulkin mallaka takeyi mutum bashi da ‘yancin yin abu saida izininta, kuma batun wuta nifa ba kwana zanyi a gidanta ba tunda naga kuliyoyi take kiwatawa”. Kusan a tare Sadik da Dije suka haɗa baki wajen cewa. “Ki daure ki riƙa yin abinda takeso zaku shirya”. Shiru kawai ta musu amma bata tunanin yin haka hira suka sake taɓawa kana daga bisani sukayi wa Yaya Abba sallama sannan suka shiga cikin gida... Akwana atashi ba wuya yau kwanakin Khausar Biyar acikin Rugar Jauro Yaya ta fara sabawa da mutanen garin Sosai Musamman ma Dije ta sun zama ƙawaye dan agidansu take kwana ita da zuwa gidan Hajja Nana sai da safe take zuwa tayi mata shara sannan duk lokacin da sukaje sukayi tatsa zasu kai mata Nono. Kasancewar duk gidajen ƙannenta taran ne ko yaushe sukayi tatsa zasu kai mata madara Shiyasa koda duk Rugar za'a rasa Madara da zuma ba'a rasawa a wurinta. Kullum da rana gidan Hajja Nana Khausar ke zuwa cin abinci saboda anan ne zata zaɓi wanda ranta keso duk sanda ta zata buɗe kwanikan ta zaɓi wanda ranta keso Hajja Nana za tace ba tasa son ƙaƙale duk wanda ta fara buɗewa shi zata ci ita kuwa khausar tace bataji abunta haka ba domin Hajja Nana ta kasance irin tsofi nan masu sa ido bata gani sai ta tanka to kullum cikin faɗa suke ko yaushe Dije na maƙale da Khausar sosai Shaƙuwa ya sake shiga tsakaninsu sai kuma Ma'u yar bappa Garga sai dai ita bata karisasu girmaba, sannan sosai take walwala domin garin ya mata daɗi sai dai kullum cikin kewar Mahaifiyarta da kuma ƙannenta take . Washe gari, da safe Khausar na zaune gefen Hajja Nana tana matsa mata ƙafa. Hajja Nana tayi saurin janye ƙafarta azabure tana watsawa Khausar kallon banza azafafe tace. “Idan ba zaki matsa min ƙafarba aise ki bari bawai kizo kina min mugunta ba”. Sheƙeƙe Khausar ke Kallonta da mamaki. Ta janye hannunta daga kan ƙafar Hajja Nana tace. “Ashe abin arziƙi yana zama na tsiya daga temako sai kiyi min ƙazafi”. Kallon Banza Hajja Nana ta warsa mata kafin tace. “Saboda baki da kunya nice zanyi miki ƙazafin?”. Khausar data buɗe baki da niyyar magana ta fasa jin Sallamar Yaya Abba zama yayi tare da gaishe da Hajja Nana cike da ladabi Amsawa tayi tana sanya masa albarka. Kallonsa Khausar tayi tace. “Good Morning Yaya Abba”. Da murmushi afuskarsa yace. “Morning Khausar how was your night?”. “Fine”. Tace tana ɗan murmushin tsokana tasan kwanan zance, Ai kuwa taɓe baki Hajja Nana tayi tace. “Wato Abba ƙafara koyon munafurci irin na baƙaƙen kafuran nan ko kazo har gaba kana zagina?”. Kai Yaya Abba ya girgiza yace. “Wallahi ba munafurci ko zagi muke ba Goggo Hajja kawai gaisawa muke”. Ta gyaɗa kai tace. “Toh adai dinga magana da yaren da zanji dan Manzon Allah (S.A.W)Yayi Hani da idan mutane na zaune wasu daga ciki su sauya harshe zuwa wanda sauran basaji koda ba zaginsu zasuyi ba amma wanda baijin Yaren zai tsargu dan haka ku kula hegiya gantalelliya mai kaɗifiri”. Kai Yaya Abba ya gyaɗa cike da ladabi yace. “Insha Allah zamu kiyaye”. Ita kuwa khausar baki ta taɓe aranta tace wannan tsohuwa ta fiye mita da takalan magana. Ta fara da fadin Manzon Allah a karshe kuma ta buge da masifa da cemin gantalelliya. Azahiri kuwa sai ta saki fursakarta ta matsa kusa da yaya Abba tace. “Ayyah Yaya Abba ka sammin wayarka zan kira Mommy na mugaisa”. Juyowa yayi ya kalleta tare da cewa. “Ok ba matsala anjima zan baki sai Khadijah ta rakaki bishiyar ƙare zancen ka kuyi magana”. Cikin jin dadi tace. “Toh shikenan Nagode”. Sallama yayi musu kana ya tafi. Da yammaci Khausar na zaune adakali Dije kuma na shara suna hira sai da ta kammala sharan Khausar ta dube tace. “Dije muje ki rakini wajen Yaya Abba in karɓi wayarsa”. Kai Dije ta gyaɗa da faɗin. “Toh”,sannan suka fice suna hira har suka isa. Yaya Abba kuwa yana ganinsu ya miƙe tare da zuwa kusa dasu Idanunsa akan Khausar yace. “Kinzo”. Kai ta gyaɗa alamar eh. Yace. “Ok mutafi nima zanje taya ƙanina Ibrahim ɗiban ƙwai”. Ɗan murmushi tayi tare da faɗin. “Yaya Abba kaima kana aikin?”. “Sosai ma aikin gado ne ai duk da cewa ina shirin kammala degree na acikin Ɓadamaya bazai hana nayi aikin gadona ba”. Cewar Abba Kai ta jinjina kana tace. “Allah yataimaka”. Ya amsa da. “Ameen”. Suna isa Gindin bishiyar Khausar ta juya ta kalli Dije tace. “Dole sai na hau bishiyar network zai zo”. Dije ta girgiza kai tace. “A'a ko kan duwatsun nan kika zauna zaki samu network inde ba'a cika ba abinda yasa wasu ke hawa bishiyar saboda kafin su zo duk an cika saman duwatsun idan kasamu ancika dole sai kan bishiyar”. Kai ta gyaɗa kafin ta ƙarasa ainihin inda ƙarƙashin bishiyar yake Sadik ta gani zaune yana waya. Murmushi ta sakar masa tare da zama gefensa sannan ta sanya number Mommy. ringing ɗaya ana biyu Mommy tayi picking. Ita kuwa khausar cike da zumuɗin jin Mommy tayi picking call ɗin tace. “Mommy na”. Aɓangaren Mommy kuwa jin Muryar Khausar yasa ta saki murmushi mai sanyi kafin tace. “Khausar”. Murmushi mai nuni da zallan farin ciki Khausar tayi tace. “Na'am Mommy na nayi missing ɗinki”. “Nima nayi missing ɗinki Mamana”. Dariya Khausar tayi tace. ”Mommy Ina Raudat?,Ina Haiydar?, Ina Ramadan??”. Murmushi Mommy tayi tace. “Duk suna lafiya”. Haiydar dake gefen Mommy yace. “Gani nan Maman Fitina nayi missing ɗinki tunda kika tafi babu mai min faɗa babu wanda zai ce na renasa sannan babu mai nuna min iko da mulkin mallaka”. Dariya Khausar tayi tace. “Hmmm ai nagane ɗan uwa ko ina nuna maka iko da mulkin mallaka gada nayi in faɗa maka na samu wacce ta cuna Ni komai da ƙa'ida akeyi ko kallo zakayi sai an maka tsarin kallon da zaka yiwa mutum shi”. Murmushi Haiydar yayi yace. “Allah Hajja Nana ko?”. Dariya tayi tace. “Ita dai fitinanniyar tsohuwa, tsohuwa sai Bala'i ba'a zaman lafiya da ita". Mommy dake gefe ta amshi wayar da faɗin. “Um,Um Khausar karfa ta jiki”. Murmushi Khausar tayi tace. “Toh idan ta jini ma ya ta iya dani bare ma tana can gida mun barta tana gyaɗa kai muku ma munzo wajen bishiyar ƙare zancenka ne ko surutunka ne ohon musu!”. Haiydar ne yayi Dariya kasancewar wayar a speaker yake yana jin komai yace. “Wani irin bishiya ne kuma ƙare zencen ka”. Ita kuwa khausar cewa tayi. “Hmm garin fa basu da network sai wajen bishiya ɗaya suke zuwa yanzu ma haka wurin bishiyar nake”. Dariya Haiydar yayi yace. “Ai dama kin iya ɗale-ɗalen bishiya kina nan kamar Biri”. Murmushi tayi sai kuma ta ɓata fuska tace. Ni sa'arkace za kace ina tsalle kamar Biri??”. Murmushi tare da faɗin. “Addah Khausar Sarkin son girma kiyi haƙuri to yar uwa”. sakin murmushi tayi kafin tace. “Bawa Ramadan”. Miƙa masa Haiydar yayi. Ramadan yace. “Addah Khausi nayi kewarki”. Cike da ƙaunar ƙannen nata tace. “Nima nayi kewarka ɗan ƙanina Insha Allah na kusa dawowa”. Amsar wayar Mommy tayi tace. “Kin Kusa dawowa haka kukayi da Hajja Nana nan?”. fuska ta ya mutsa kana tace. “Sai munyi da ita Mommy yau kwanana biyarfa ana shida nake idan nayi sati biyu zan dawo ai”. Mommy tayi murmushi tace. “Tsakaninku de ni yanzu ba ruwana nima ba bari na tayi ba”. Dariya Khausar tayi tace. “Ina Raudat? Su Ramadan na zuwa hadda ko?”. Kai Mommy ta gyaɗa tace. “Ai Asma'u ma tazo tace malamai nata tambayarki sunce taya zakiyi tafiya baki sanar musu ba kodan ba boko ne sai hadda ne kawai wato?”. Girarta ta ɗan shafa da yatsarta manuniya kana tace. “Hmmm ai kuwa na faɗawa Asma'u ta sanar musu wataƙil ta manta ne” “To ai yanzu kam sai in kin dawo. Ki dai bi tsohuwar ahankali saboda ki samu tabarki ki dawo akan lokaci”. Cewar Mommy. Itako Khausar kai ta gyaɗa kafin tace. “Toh shikenan Mommy na zanyi duk yanda kika ce. Yawwa Mommy ki turo min Number Ummin Asma'u”. ”Toh”Mommy tace sannan ta katse kiran. Ita kuwa Khausar juyawa tayi tare da kallon yaya Abba dake tsaye ta langwaɓar da kai kafin tace. “Ayyah Yaya Abba in ƙara Kiran wata ƙawata?”. Kai ya gyaɗa kana yace. “Ki kira ba matsala”. “Toh”, tace tare da maida kallonta kan wayar da text ɗin Number ya shigo copy tayi tare da dearling. Tana kira ringing ɗaya Ummi ta ɗauka. Khausar tace. “Ummina”. Murmushi Ummi tayi tace. “A'a Khausar kece? Ya mutanen Ruga fatan kun same su lafiya?”. “Lafiya lau Ummi. Ina Asma'u”. Cewar Khausar “Gata nan tana tsifa”. Ummi ta faɗa tare da miƙa wa Asma'u wayar. Asma'u na amsar wayar ta maƙala akunnenta tare da ƙyalƙyalewa da dariya tace. “Na sani”. Ita kuwa Khausar hararan wayar tayi jin Dariyar da Asma'u keyi tace. “Kinsan me?”. Asma'u tace. “Na sani tsoron Yah Moddibo kike yasa kika gudu kika tafi Rugar nan inba haka ba keda baki ƙaunar tafiyar nan amma daga arba dashi kika tafi Ruga”. Ƙwafa Khausar tayi tace. “Ba dole in tafiba tunda kika kaini kafin in dawo wala Allah ya huce”. Cike da zolaya Asma'u tace. “Wai ai Yah Moddibo baya mantuwa duk abinda aka masa". Wara ido Khausar tayi sai kuma tace. “Asma'u duk kece kika janyo min da baki kaini gidansu ba da haka bai faru ba wlh”. Asma'u kuwa murmushi ya subce mata kafin tace. “Calm down wasa nake Miki shi idan abu ya wuce kwana uku ma wata ƙil mancewa”. Ita kuwa khausar jin haka yasa ta saki ajiyar zuciya da faɗin. “Alhamdulillah". Sai kuma ta harari wayar tare da cewa. “Au wata ƙil nema kenan”. Dariya Asma'u tayi kana tace. “Yaushe zaki dawo?” Taɓe baki Khausar tayi tace. “Waya sanma wannan tsohuwar wataƙila nan da sati biyu ko kuma sati ɗaya idan nayi sa'a tabarni in dawo anata wuceni ahadda ko?”. Da sauri Asma'u tace. “Eh ana wuce ki kam”. Ita kuwa Khausar ɗan jim taui kafin tace. “Insha Allah nima dai na kusa dawowa”. “Toh Allah yasa”. Asma'u ta faɗa kana sukayi Sallama tare da katse kiran. Kallon Khausar yaya Abba yayi yace. “Koda kuna hutun ana baku hadda ne?”. Kai ta gyaɗa da faɗin. “Eh Yaya Abba muna zuwa hadda”. “To ai babu matsala inde hadda ne ki riƙa zuwa wajen Babanmu yana ƙara miki ai zai baki hadda ki cigaba kada awuceki”. Cewar Abba. Khausar kuwa cike da farin ciki tace. “Toh shikenan Yaya Abba insha Allah kuwa”. Daga haka suka miƙe suka taho kai tsaye gidansu Abba suka nufa bakinsu ɗauke da Sallama suka shiga. Kallon Dije da Ibrahim Yaya Abba yayi yace. “Bari na rakata wajen Liman”. Kai suka gyaɗa sannan yayiwa Khausar jagora zuwa ɗakin Mahaifinsa bakinsu ɗauke da Sallama suka shiga ɗakin. Ɗaki ne irin na bukka mai shatin kwabo baki ɗaya ɗakin kewaye yake da littattafan Addini kana da qura'anai bugu da ban bugun misira da warash. Cike da ladibi Khausar ta gaishesa Amsawa yayi cikin sakin fuska kafin ya kalleta da murmushi yace. “Matso mana”. Kai ta gyaɗa tare da Matsawa kusa dashi ta zauna akan buzunsa. Yana murmushi yace. “Lafiya? ko dai ƙaran Addata kika kawo?”. Murmushi tayi tace. “Ni Meye ruwana da ita da zan kawo ƙaranta, dama karatune muna hadda Acan toh kuma na tsaya za'a iya wuceni”. Kai Ya jinjina kana yace. “Wacce surah kuke?”. Anutse tace. “Suratul Taubah muke munyi shafi huɗu zan tashi ashafi na biyar”. Cikin gamsuwa ya gyaɗa kai tare da faɗin. “Karanta inda kukayi naji”. Gyara zamanta tayi tare da gyaɗa kai kana taja sassayan numfashi cikin zazzaƙan Muryanta tayi basmala kana ta fara rerewa karatun cike da jan Tajwidan Tartilan. Kai Malam Liman ya jinjina da faɗin. “Masha Allah”. Yaya Abba kuwa lumshe Idanunsa tun lokacin data fara karatu kana ya buɗe su alokacin da takai ƙarshen ayan yace. “Masha Allah Allah ya baki zaƙin murya Hafiza”. Jin abinda yace. Yasa Khausar sakin sakin ɗan guntun murmushi Malam Liman ne yace. “Masha Allah, yanzu dai kullum ki ringa zuwa irin wannan lokacin kina ɗauka darasin saboda maza basu fara zuwa ba, dalibai yara kuma sun tashi. kullum zan dinga baki awa ɗaya sai ki dinga zuwa ina ƙara miki sannan da wasu littattafan ma idan kunayi ki faɗa zan dinga ƙara miki”. Cikin daɗi tace. “Toh ba matsala Insha Allah sannan munayin littafin Tajweed, Tauheed, Urasatul Nurul yaƙin, Nahwu, da kuma Mi'atu Hadith da dai sauransu”. Gyara zaman babbar rigarsa yayi tare da faɗin. “Insha Allah zaku riƙa zuwa ina ƙara miki keda Dija da Ma'u tunda dama sunyi sauƙa”. Sannan ya buɗe kur'ani ya miƙa mata shi kuma ya shiga karanta mata akai yayin da yake bin ko wanne harafi yana basa haƙƙinsa saida yakai har ƙarshen shafin kafin ya dubeta yace. “In mai-maita Miki?”. Kai ta girgiza alamar a'a tana jinjina baiwar ilimi da zaƙin murya da Allah ya masa. Anutse yace. “Ki hadda ce su kafin gobe sannan ki kawo min”. Khausar kuwa kai ta gyaɗa tace. “Insha Allah zan dage Malam amman dai goben ma zan biya sai jibi a ƙara min ko?”. Murmushi yayi tare da cewa. “La ba'as”. Miƙewa tayi Sannan tace. “Zan tafi da Kur'anin”. “Toh” ya cemata Sannan suka fice bayan fitansu ta dubi Dije tace. “Muje gidan garkuwan rugan ki”. Murmushi Dije tayi tace. “Gidan Baffa Umaru”. Kai Khausar ta gyaɗa sannan suka nufi gidan Baffa Umaru. Aƙofar gida suka samesa yana tare da baƙi, Juyawa yayi ya kallesu kafin yace. “Kushiga ciki ina zuwa". Kai suka gyaɗa sannan suka shiga cikin gidan bakinsu ɗauke da Sallama,kallon cikin gidan Khausar tayi ko ina ashere fes-fes babu alamar datti ko ƙazanta. Adama kuwa murmushi fuskarta ta faɗaɗa tace. “Su Khausar ne sannun ku da zuwa”. Dije tace. “Yawwa Goggo Adama ya gida”. Ta amsa da lafiya lau sannan ta miƙe ta kawo musu faten doya da ruwa arandan ƙasa mai sanyi. Ita kuwa khausar murmushi tayi tana jinjina mutunci da karancin Goggo Adama atare sukaci kana suka gabatar da sallan Azahar sannan sukayi mata har zuwa lokacin Baffa Umaru bai shigo ba. Bayan fitarsu agidan Baffa Umaru Khausar ta juya ta kalli Dije tace. “Muje gidan Hajja Nana in ɗauki kayana”. Dije tace. “Toh”. Sannan suka nufi gidan Hajja Nana ba suyi wani tafiya mai tsawo ba suka isa gidan, Atsakar gida suka tarar da Hajja Nana. Harara Hajja Nana ta watsa mata tace. “Ke kam Uwar gantali kina nan kina ta yawo bazan ganki ba bare in Zauna dake”. Fuska Khausar ta ɓata da faɗin. “Wani irin gantali duk ba gidan ƙannenki da ‘ya‘yanki nake zuwa ba kuma ɗazun nan ina anan na tashi zaki ce amma yanzu zaki ce min gantali na tafi to nide gaskiya ba gantalalliya bace yawwa zaki wani cemin gantali ba gidan ƙannenki na tafi ba kuma saida na faɗa miki zamuje Bishiyar ƙare zancenka in kira Mommy na sannan yanzu ki wani cemin gantalalliya to nide wallahi ba gantalalliya bace”. Hajja Nana tace. “Ke kam wace gantalalliya ce ma ta fiki?,In banda gantali me kika iya?". Ita kuwa khausar juya manyan Idanunta dake lumshe kafin tace. “Wallahi da abinda na iya”. Hajja Nana kuwa kai ta gyaɗa tace. “ƙwarai da abinda kika iya fitsara ba gashi ma yanzu kina yi bayan shi babu wani abu da kika iya”. Khausar za tayi magana Dije tayi saurin riƙe hannunta cikin ƙasa da murya tace. “Dan Allah kiyi shiru ki ƙyaleta”. Kai ta gyaɗawa Dije tare da tsuke bakinta. Hajja Nana kuwa fuska ta tsuke Idanunta akan Khausar tace. “Bari in samiki doka gidan Jauro da kike zuwa ki kwana bazan hanaki ba tunda kince kinfi farar kura tsoro. Amma gobe ana sallar asuba na ganki anan dan zaki riƙa tayani aiki. Baki Khausar ta taɓe da faɗin. “Allah ya kaimu sannan bawai ana idar da Sallah bane zanzo saina yi Azkharul sabah da kuma karatuna”. Harara Hajja Nana ta watsa mata tace. “Toh Al-huda-huda sarkin karatu”. Khausar kuwa baki ta taɓe tace. “Koma de menene”. Sannan ta juya ta shiga ɗaki ta dauko kayanta tana fitowa ne taji Hajja Nana na cewa Dije. “Kar kice zaki koyi rashin kunyar wannan yarinyar". Dije kam murmushi tayi ita kuwa khausar batare data tanka taba ta fice Dije tabi bayanta... GEMBILA Acan ɓangare Moddibo kuwa kwance yake akan makeken gadonsa daya sha shimfiɗa na Alfarma yayin da hannunsa biyu ke haɗa yana addu'ar bacci ya ɗauki kimanin minti goma kafin yasha fa addu'ar ya gyara kwanciyarsa yana mai lumshe idanunsa da haka bacci ya ɗauke sa can cikin baccinsa yaji wayarsa na ruri ya buɗe idanunsa kasancewar sa ba mutum ne mai nauyin bacci ba yasa hannu ya janyo wayar yana kallon screen ɗin Bahrain shine sunan dake ƙasan screen ɗin. Picking Yayi tare da kai wayar kunnensa tare da sallama. Amsawa Jalaludeen yayi da faɗin. “Ya yatsun ƙafar naka sun warke ne!?”. Moddibo kuwa gyara kwanciyarsa yayi da faɗin. “Jameel ya faɗa maka kenan?". Jalaludeen yace. “Kamar dai baka sanni ba sai Jameel ya faɗa min zan sani?”. Moddibo kuwa kwanciyar sa ya gyara kana yace. “Eh ainaga kunyi waya ne bayan abin ya faru”. Jalaludeen yace. “Wallahi Jameel bai faɗa min ba lokacin da abin yafaru ma ai ina nan”. Shi kuwa Moddibo kwanciyarsa ya gyada tare da faɗin. “Hmmm yayi kyau ka kawo mana ziyara kenan”. “Eh nakawo muku ziyara Barka da jumma'a ai tare mukayi jam'in sallan jumma'a ma”. Sassayan numfashi Moddibo ya fesar kana yace. “Mungode amma aiba mu gaisa ba". Murmushi Jalaludeen yayi yace. “Ai zamu gaisa sai kuma na samu abin kallo ana dramer Shiyasa ba mugaisa ba, na tafi shi Kam Jameel baima San nazo ba Dan ban faɗa masa ba”. Kai Moddibo ya jinjina kafin yace. “Toh yayi kyau ya labarin mutanen England”. Jalaludeen yace. “Duk suna nan lafiya”. Kana sukayi Sallama. Kallon screen ɗin wayar Moddibo yayi Aransa yace Allah mai kyauta shi Jalaludeen jinsinsa da ban amma haka yake jin daɗin Mu'amala damu sannan babu cutarwa atsakaninmu da wannan tunani bacci ya ɗauke sa. Acan Rugar Jauro yaya kuwa Washe gari da Asubah bayan Khausar ta idar da Sallah tayi Azkharul sabah da tagama ta juya tare da kollon Dije tace. “Muje gidan Hajja Nana”. Dije tace. “A'a kije Ni zan dafa mana abinda zamu ci kinga Goggo Nanne bata jin daɗi”. Kai Khausar ta gyaɗa sannan ta miƙe ta fita atsakar gida ta samu Hajja Nana ta jiƙa wankekkdn wakenta ya jiƙa, Zama Khausar tayi tace. “Ina kwana Hajja Nana”. Ba yabo ba falassa Hajja Nana tace. “Lafiya". Sannan ta ɗaura da cewa. “Ga can wake ki ɗauka ki markaɗamin acan”. Ta ida maganar tana nunawa Khausar inda ta kafa dutse irin na mutan da saboda basu da inji agarin". Ita kuwa khausar inda Hajja Nana ta nuna mata da faɗin zatayi markaɗe ta riƙa bi da kallo kafin ta mayar da kallonta kan Hajja Nana tace. “Wai in markaɗa Miki me?”. Hajja Nana tace. “Waken ƙosai kinga kwana biyu banyi ba tunda kika zo Mai nane ya ƙare sai jiya na samu da Sadik ya shiga Gembila ya sayo min”. Ita kuwa khausar da Mamaki tace. “Kamar ya in miki markaɗe?”. Kallonta Hajja Nana tayi tace. “Kiyi min markaɗe nace”. Ita kuwa Khausar ƙugu ta riƙe tace. “Ni wallahi ban taɓa ganin yanda akeyi ba ban sani ba kuma ban iya ba”. Hajja Nana kuwa sheƙeƙe ta dubi Khausar tace. “Insaki aiki kice baki iya ba?”. Baki Khausar ta tura tare da riƙe ƙugu tace. “To ban iya ba ya za'ayi na iya ni Wallahi ba zanyi ba taya ma nasan zan iya riƙe dutsen nan nace zanyi markaɗe kije ki kirɓasa aturmi mana kawai”. Haɓa Hajja Nana ta riƙe cike da mamaki tace. “Ni kike cewa Inje in kirɓa aturmi Meye amfaninki Kai Allah wadaran naka ya lalace ke kam ba irin Addarki ba sam”. Ita kuwa khausar hannunta ta harɗe aƙirji Idanunta tsaye akan Hajja Nana tace. “Toh yanzu tunda kinsan Ni ba irin Addah bace sai kiyi min hakuri Addah na agabanki ta girma duk wani horonki ta iya Ni Kuma ba agaban ki na girma ba, kuma ban iya ba ya za'ayi kice min haka wata ƙil ma bakya tuna ta kiyi mata addu'a sai in magana irin haka aya tashi kike tunata”. Dafe ƙirji Hajja Nana tayi da faɗin. “La'ilah ha ilallahu Muhammadu Rasulullah (S.A.W) Khausar ni zaki nunawa son Nanne?”. Ita dai Khausar na riƙe da ƙugu sannan tace baza tayi markaɗe akan dutse ba. Suna nan atsaye haka Baffa Umaru ya shigo ganinsu tsaye ahaka yasa yace da Khausar. “Lafiya kuwa”. Fuskarta babu walwala tace. “Wai Hajja Nana ce saina yi mata markaɗe akan dutse Ni kuma ban iya ba”. Baffa Umaru kuwa juyawa yayi ya sake kallon Hajja Nana yaga sai wurgawa Khausar Harara take Kallonsa ya mayar kan Khausar yace. “Ayyah Khausar ki gwada mana ba aikin mata bane”. Da sauri tace. “Toh ban iya ba Baffa Umaru taya zan gwada”. Hannunta ya riƙe tare da faɗin. “Zo in koya miki”. Ba musu ta matsa kusa dashi ɗan dutsen ya ɗauka ya kafa sannan ya matso da roban waken ya ɗibi wake cikin hannunsa yace. “Ki markaɗa”. Ta gyaɗa masa kai sannan ta fara Markaɗawa ga mamakinta sai taga yana markakaɗuwa har tayi niyyan zagewa ta markaɗa sai ta fasa ta fara jefar da ɗaɗɗaya tasan muddin tayi mai kyau Hajja Nana zata mayar dashi aikinta baya ga haka kuma daga riƙe dutsen yatsun hannunta sun sage tun lokacin data faɗo daga bishiya agidansu Moddibo hannunta bai dawo dai-dai ba. Ganin tana jefer da waken da guda-guda yasa Hajja Nana cewa. “Hegiya gantalelliya kibar min abuna”. Ta ƙarashe maganar tare da amsar dutsen tashiga markaɗawa. Miƙewa Khausar tayi tare da kaɗe hannunta tace. “Yafi Nono fari”. Shi dai Baffa Umaru murmushi yayi tare da yiwa Hajja Nana sallama ya tafi, Ita kuwa Khausar saurin bin bayansa tayi suka tafi adai-dai ƙofar gidan Malam Liman suka tsaya tagaishesa cike da ladabi. Sannan suka cigaba da tafiya suna taɓa hira har suka isa gidansa. Adda Adama na ganinta ta sakar mata murmushi tare da faɗin. “Khausar sannu da zuwa ya gida ya gajiyarku na jiya?”. Murmushi tayi da faɗin. “Ba gajiya Adda Adama ya Aiki”. Ta amsa da. “Alhamdulillah. Kana tace. “Ke kam tunda kika zo baki taɓa zuwa kin kwana mana ba”. Khausar na gyara zama tace. “Insha Allah yau zan zo mukwana”. Murmushi Adda Adam tayi da faɗin. “Aikam Nagode”. Khausar ta juya tare da kallon Baffa Umaru dake sakin murmushi tace. “Amma fa ki faɗawa jarumin mijinki ya kawo min abu mai daɗi”. Murmushi kana tace. “Inde wannan ne baki da matsala”. Bayan sun gama hira tayi musu sallama ta tafi. Da daddare bayan sun idar da Sallah Isha'i Khausar tace da Dije. “Muje gidan Garkuwan Rugarku mu kwana”. Dije tace. “Toh muje”. Sannan ta miƙe suka shiga ɗaki sukayi wa Goggo Nanne sallama. Adda Amada dake ɗaki tana jin Sallamar su ta fito fuskarta ɗauke da murmushi tana cewa. “Ai yanzu nake cewa zanbi sawunku”. Khausar tayi murmushi tace. “To aigamu ina Jarumin mijin naki?”. “Yana nan mai zaki bashi?”. “Babu abinda zan bashi abin daɗi da yace zai ajiye min zai bani idan kuma babu in tattara in tafi”. Ta Ida maganar tana murmushi. Miƙewa Adda Adama tayi tace. “Toh ki kwantar da hankali ga abin daɗi”. Tayi maganar tana ajiye musu karamin kwandon kaba dake ɗauke da Inabi, Tuffa, Mangoro, Ruman, da sauran kayan itatuwa sai kuma kwanon farfesun kifi yana tururi. Murmushi mai sauti Khausar tayi tace. “Lallai yana yina ashe wannan gara haka”. Ita dai Dije murmushi kawai take musu. Duka suka haɗu suka ci sannan suka kwanta ɗaki ɗaya da Adama. Shiko Baffa Umaru yana can aɗakinsa ya kwana. Misalin ƙarfe biyu na dare Khausar ta farka aɗan firgice sakamakon hayaniya da take jiyowa. Dije ta gani itama zaune tana zazzare idanu ganin sukayi Adda Adama ta fice aɗakin da mugun sauri suma cikin sauri suka bi bayanta. Da gudu Adam ta nufi ɗakin mijinta dai-dai lokacin daya fito. Hannunsa ta riƙe cikin raunin murya tace. “Dan Allah kada ka fita da alama suna da yawa kaji hayaniyar su”. Da sauri ya juya ya kalleta tare da faɗin. “Idan ban fita ba wa zai dakatar da su wannan daga ji mutanen Ƙauyen Garinga ne bamusan mai suka zo dashi ba dare dare zasu zo mana haka babu yanda za'ayi dole in fita”. Ta girgiza kai tare da riƙe sa kana tace. “Dan Allah kada ka fita". Tureta yayi daga jikinsa ya fita yana fita ya hango Arnan mutanen Garinga ne wanda yawansu zai kai kimanin mutum ɗari da sauri ya nufi hanyar jejin yayin da bayansa ke rataye da kwari da baka hannunsa na riƙe da touch light mai masifar haske. Cikin fushi da tsawa ya haskasu da touch light ɗin hannunsa mai masifar kashe ido yace. “Menene wai ma tukun ina kuka nufa!?”. Ɗaya daga cikinsu wanda ya kasance babban su yace. “Ƴar mu muke nema ta ɓata”. Duk da acikin duhu ne hakan bai hana shi watsa musu kallon banza ba yace. “Ƴarku ta ɓata shine dare-dare haka zaku zo wajenmu nemanta?”. Biyu Daga cikin su suka ce. “Ai kidnapping ɗinta akayi”. Afusace yace. “Kuma in kidnapping ɗinta akayi sai akace muku tana nan Rugarnu?”. Babban cikinsu yace. “Tana nan Rugarku dama Fulanin ku ai sune suka sace ta suka kawota dan haka an saceta tana nan mu nan muke zargi”. Cikin tsananin fushi da zuciya Baffa Umaru yace. “Baku isa ba babu yanda za'ayi haka ya faru!”. Babban cikinsu yace. “Dole sai mun shiga garinku gida-gida ɗaki-ɗaki mun bincika”. Cikin tsananin fusata Baffa Umaru yace. “Wallahi in dai ina raye baku isa ba babu wanda ya isa yashiga garinmu yace yayi bin cike indai haka kuke so kuje kuzo da rana muyi magana”. Babban su yace. “Mu adaren nan muke so muyi magana”. Baffa Umaru yace. “Toh baku isa ba”. Dumfaro sa sukayi da niyyar shiga Rugar gadan-gadan. Shi kuwa baya yaja tare da jan kwari da baka yace. “Duk wanda yake jin shi Jarumi ne kuma ya kai to ya kuskura ya shiga mana cikin Ruga yaga abinda zai faru”. Tsayawa su kayi akuma dai-dai lokacin ne sauran mazan cikin Rugar suka fiffito mafi yawa ma sautin Baffa Umaru ne ya tashe su dan shi mutum ne mai zafin gaske musamman ma idan ransa ya ɓaci. Acan bakin ƙofar gida kuwa sosai Khausar ta shiga mamaki sai asannan ta tabbatar da maganar Adama da tace mijinta Jarumi ne kuma Garkuwan Rugar. Malam Liman ne yayi gyaran murya bayan isan su wajen yace. “Tun da kunce haka yanzu ku koma da safe sai kuzo aje wajen Mai gari sai ayi magana”. “Toh”, Babban su yace sannan suka juya suka tafi badan ransu ya soba. Washe gari da safe bayan sunyi ta tsansu sun daddawo da hantsi Arnan garin Garinga suka zo suka haɗu aƙofar gidan Jauro. Bayan sun gama gaisawa Jauro ya dubesu Anutse cike da kamala irin na shugaba yace. “Mai yafaru muna sauraron ku". Babban su yayi gyaran murya yace. “Ƴar muce buke ce akayi kidnapping sannan muna zargin tana cikin wannan Rugar”. Cikin danne takaicin ƙazafin da arnan ke son yi musu Jauro ya jinjina kai kana yace. “Kun tabbatar tana cikin wannan Rugar?”. Kai Babban su ya jinjina yace. “Ƙwarai mun tabbatar sannan mun zo zamu shiga Umaru ya hana mu sannan Umaru shi yake sa mana Ido komai akayi bamu isa muyi magana ba sam Bama ƙaunar abinda Umaru yake mana yayi rayuwarsa muyi rayuwar mu!”. Wani banzan kallo Baffa Umaru ya watsa musu cikin yanayin zafinsa yace. “Ba zanyi rayuwata kuyi rayuwarku ba muddin kuna so nayi rayuwata kuyi naku to ku fita sabgarmu banga wanda ya isa ya shigo cikin Rugar mu yace zai taka mu inbar saba”. Da sauri Jauro ya ɗaga masa hannu hakan yasa Baffa Umaru yayi shiru. Baffa Jauro kuwa maida kallonsa garesu yayi kan yace. “Munji mun yarda an sace muku yarinya anyi Kidnapping ɗinta”. Sai kuma ya maida kallonsa kan Malam Liman yace. “Ɗauko mana Bible agidanka”. Kallon Yaya Abba Malam Liman yayi yace. “Jeka ɗauko min asalin Bible na da acikin littatafai na”. Miƙewa Yaya Abba yayi babu daɗewa ya dawo hannunsa riƙe da Bible ɗin ya mikawa Jauro. Karɓa Jauro yayi tare da miƙawa Babban su yace. “Gashi ku rantse da littafin ku tunda kuce ƴarku ta ɓata kuma tana garin nan”. Ƙin amsa Babban su yayi. Cikin sanyi Jauro yace. “Inde ka tabbata ƴarku ta nan to ka karba ka rantse Inde ka rantse. To mukuma zamu baku damar shiga sannan muma zamu rantse da Alkur'anin mu mai girma cewa ‘yarku bata nan amma duk da haka idan kun rantse zamu baku damar shiga cikin gida-gida ɗaki-ɗaki kuyi bin cike”. Shi dai babban nasu kin rantse wa yayi sai wuƙi-wuƙi yakeyi da ido. Ganin haka yasa Jauro ya kalli sauran na bayansa yace. “To ɗaya daga cikin ku ya karɓa ya rantse”. Still suma ƙin karɓa sukayi. Afusace Baffa Umaru yace. “Ba gashi ba basu da gaskiya Arnan nan neman fitina suke damu sam babu gaskiya alamarin su bayan sace-sacen dabbobi da kuke mana sai kun nemi fitina damu”. Babban su ya juya ya kalli Baffa Umaru yace. “Wani irin sace-sace kuma?". Harara Baffa Umaru ya watsa masa yace. “kana tunanin bamusan kune kuke sace mana dabbobin muba to yanzu ga Bible ka karɓa ka rantse da littafin ku cewa ƴarku ta ɓata duk alamun rashin gaskiya ya bayyana atare da ku kawai ku taru dare-dare kuzo mana da mugun nufi”. Anutse Jauro yace. “Umaru kayi haƙuri kaki”. Yasan idan ransa ya ɓaci babu wanda zai iya shawo kansa. Malam Liman ya dubesu yace. “Tunda har baku rantse da littafin kuba kenan ƴarku bata ɓata ba in kuma ta ɓata to baku da tabbacin tana garinmu”. Babban su yace. “Shikenan babu matsala tunda zaku iya rantse wa da littafin ku munsan bata Rugarku yanzu magana ya ƙare. Amma Jauro da malam Liman ku jawo Umaru kunne ya fita sabgarmu”. Miƙewa Baffa Umaru yayi tare da nuna kansa da hannu yace. “Ni ɗin nan ka ganni nan Babu wanda nake tsoro sai Allah daya hallicceni". Ƙwafa Babban su yayi yace. “Tun da haka kace shikenan amma zaka ga abinda kake tsoro”. Da sauri Jauro ya juya ya kalli Babbansu yace. “Mu ba mason fitina me kake nufi da zaiga abinda yake tsoro?”. Babban su yace. “Indai zai shiga sabgarmu to zaiga abu da yawa”. Jauro yace. “Toh bama son fitina tunda kuda kanku kun tabbatar da ‘Yarku bata cikin Garinmu sannan kuda kanku kunsan baku da gaskiya kun ƙi ku rantse, karku sake shigo mana Rugar mu haka ba maso idan kuma kuka sake to zamu haɗa ku da Sarkin cikin Gembila”. Jin Jauro yace zai haɗa su da Sarkin Gembila yasa suka ce. “To ayi hakuri ba zasu sake ba”. Sannan suka juya suka tafi cike da baƙi ciki badan Umar daya hana su shiga ba adaren da sun samu damar kwasan dabbobi damar saboda haka suka ce ansace musu ‘yarsu. Bayan kwana biyu Komai ya lafa ba fitina da hantsi Khausar da Dije da Ma'u sun ɗebo kayan marmari arafi suna fitowa daga cikin rafin suka hango wata mota fake agefen Rugar tasu sai kuma hango wasu mutane biyu ɗaya ya fito daga gefen dama ɗaya kuma daga gefen hagu da gudu suka shiga motar kafin su Dije su ƙara so sun figi motar. Khausar kuwa sosai tsura fuskokin su ido kafin su shiga motar, sosai ta riƙe kamanninsu. sannan tabi motar da kallo lokaci ɗaya ta riƙe Number motar Dije da sauran 'yan matan kuwa mamaki suka shiga yi shin mai ya kawo masu motar garin sannan mai yasa da suka gansu suka gudu bayan sun san a irin wannan lokacin, duk mazan garin basa nan makiyaya sun tafi kiwo saura kuma su tafi jeji wa'anda ke rafi kuma sun tafi lambu jiki Asanyaye suka tafi. Bayan kwana biyu da daddare Khausar na bacci, yayi da take ta takurewa wuri ɗaya sabida wani irin masifeffen sayin da ake tsula musu. A hankali taja dogon numfashi kana ta fesar a hankali tayi lib. Can cikin baccinta kuwa cikin wani ƙaton fili mai yalce da yashi fari ƙal-ƙal tana zaune bisa wani dutse tana fuskantar yamma kana daga bayanta kuma wani garden ne mai masifar kyau da girma babu kalan bishiya da sirran da baya ciki, wani irin ni'imtaccen iskane mai cike da ƙamshi furanni ke buso masu wata irin iska mai ɗan karen sanyi. Gefen damanta ta juya ga mamakinta M Jameel ne zaune bisa wani dutse yana murmushi, da sauri ta juya gefen hagunta kuma, Adda Adama ce ta gani zaune bisa dutse tanata murmushi. A can gabanta kuwa Mod....! *NO EDITING* *Kuyi haƙuri sai yanzu na samu caji gashi ba editing. KUNSHA TYPING ERRORS* By *GARKUWAR MARUBUTA* [19/07, 7:44 PM] Halimatu A/rahman Sadeeya: 📝🍇✨💫⏰🤴🏻👹❤️❤️❤️🍇 *SAKAYYAH* _Page 7_ _NA_ *AYSHA ALIYU GARKUWA* 🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 *FREE PAGE NE YAN UWA, BA WAI FREE BOOK BANE! INA GAMA SAKIN FREE PAGE, KO KINGA an fiddashi waje na satane. Na kuma Yaseen ne doguwa. Dan haka ki biya ki karanta cikin Aminci ba haƙƙin wani a kanki 1k ne kacal 0661110170 GTBank AISHA ALIYU GARKUWA, sai ki turo min shaidar biyanki ta WHATSAPP 09097853276. Littafin SAKAYYAH na kuɗine ƴar uwa biya ki karanta* *WOHOHO IN KAJI ANA ƘI GUDU TABBAS SA GUDU NE BEZO BA* _Ina kuke Ma'aurata masu sha'awar ganin sun zama taurari kuma fitilu a idanun mazajensu Uwar gida,Amarya,Tsakar gida,hadda tan kaɗen gida Shararriya kuma ƙasaitacciya data saba kawo muku nau'ikan sirrin sahihan magungunan ma'aurata wato *AYSHA ALIYU GARKUWA* Garkuwar Marubuta ayau ma ta dawo muku da Ingantattun magungunan mata masu kyau da inganci domin gyara kanki ki zamto tauraruwa a idanun mijinki...Muna da Ingantattun Abubuwa kamar haka_ :_Munada Garin mallaka, garin maɗi, garin Hakkin mayi, garin ɓelɗamhi Garin ilanwaddihi, Gumbar da ba'a baiwa mai kishiya, Gumbar kolli mai kellin al'khairi, Gumbar Riɗi wato 3 in 1, Gumbar makwaranyi, Masin Maliƙi mai masifar ƙarfi da matse mace wanda bani da haufi kansa 7k ne kacal sai dai yar musilar robace., Kana masin Daɗi har Maɗigan yana da masigar kyau da tsatstsafo da ni'ima, wlh wasu in sunyi amfani dashi pan biyu sabida yadda zakiyi ta tsiyaya. 5k ne Akwai, kwanon ƙasaitacciyar mace mai masifar kyau da ratsa jiki da samar da inƙantacciyar ni'ima yanada abubuwa masu kyau haɗinsa 8k ne, Zumar goron tula mai masifar kyau, tsumin dabino, mai ratsa jiki, tsumin Riɗi mai ƙarfi, Furar Mata mai tsastsafo da ni'imantaccen damshi, Cida kaza, Ciccibi Abodi, Tsumin Ɓaure, tuwon ɓauren, kana akwai maganin sanyi sadidan wanda wlh koda sanyin cikin mahaifane fes yake wanke shi kuma ko mai ciki zata shashi baida illa, kama budurwa ko bazawara duk zasu iya sha harma da yara. Set ɗin da 10k ne innkuma za'a sa miki komai rabi-rabi ne 5k ne, da dai sauransu...Se kuma fannin ƙamshi kasance da Shu'umin ƙamshi wanda ze gigita ƙwaƙwalwar Oga tare da jin ko wacce mace bata kaiba...._ _Shin ko kina da labarin Miskilinci da ƙasaitar Rayyan Naaan amma lokaci ɗaya ya zamto zautacce sakali akan soyayyar Jannart bakomai Jannart ta riƙe ba face sirrinkan gyara da kuma shu'uman humran da kulaccar sirri na Aysha Aliyu Garkuwa(Tubali) tabbas taga tasirin haka domin Naanunta ya zame mata tamkar bawa_ _Shin ko kinsan sihirtaccen haɗin da Aysha ke sha kenan ta zamto tauraruwa a idanun Hamma Yusuf(Miwasmiti)...Tabbas Mahmud ya zamto zautacce kuma makaho akan sauyayyar Bazawara wato khadijarsa duk da kuwa gashi da budurwa(Namiji Baya Kaɗan) ko kinsan hakan nada alaƙa da amfani da sahihan maganin da kuma shu'uman humran Aysha Aliyu Garkuwa??.Nasan ba zaka ku manta da irin kima da kuma darajar da Aysha ke dashi acikin Idanun Sheik Jabeer ɗin ta duk da kuwa shekaru sunja anma jinta yake tamkar budurwa 'yar sha bakwai(Garkuwa) sirrin hakan na tare da Ingantattun kuma sahihan magungunan Aysha Aliyu Garkuwa Wato Garkuwar Marubuta da kuma Ma'aurata na tabbata kunsan da cewa basirarta ba'a iya rubutun littafi ya tsaya ba hadda inganta rayuwar ma'aurata ta hanyar kawo musu Nagartattun abubuwa Ga duk wacce ta shirya saya seta tuntuɓi number ta 09097853276 muna iya tura kayan mu aduk inda kuke afaɗin Nigeria harma da ƙetare Dan Allah 'yar uwa idan baki shirya siyaba kada kiyi min magana muɓatawa kanmu lokaci...._ 🤝🏻🤝🏻🤝🏻🤝🏻🥰😘sai.kunzo. sayan na gari maida kuɗi gida, Moddibo ta hango zaune a gefen gabas yana fuskantar tata, bima'ana yana kallon yamma, zaune yake akan wani dutse mai masifar sheƙi kana wasu mutane biyu na tsaye gefen hagu da damansa, Sannan da buta gabansa bisa alama Al'wala yayi domin farin yashin daya mamaye wajen daga gabansa a jiƙe yake, kana yana mai fidda wani irin ni'imtaccen ƙamshi maisa ɗan Adam lumshe ido. Baki ɗaya haske ya mamaye ilahirin filin wajen hakan yasa itada Moddibo suna fuskantar juna yayin da M Jameel da Adda Adama matar Baffan Umaru suma ke fuskantar juna. Kana lambu dake can bayanta kuwa yake feso musu iskar yammaci dana lambun suka haɗu waje ɗaya daga sama kuma rana ne yayi Ja yana shirin faɗuwa. A hankali ta sauƙe numfashi mai nauyi tare da lumshe idanunta. Da sauri ta buɗe idanun nata, jin wani irin sassayan sautin dariya mai cike da shauƙi da Moddibo yakeyi. Cike da mamaki duk suka zuba mishi idanu. Yayinda Adda Adama ma tuni ta fara dariya mai sauti. Ita kuwa Khausar haka nan taji jikinta yana tsuma tare da sakewa, da sauri ta juya ta kalli M Jameel ga mamakinta shima ita yake kallo, da idonshi ya nuna mata Moddibo yana mai yin lallausan Murmushi, da sauri ta maida kallonta kan Kekkyawar fuskar Moddibo, wacce tunda take a rayuwarta dashi bata taɓa ganin yayi dariyar da har haƙoransa na gaba zasu baiyana ba. “Fatabarakallahu fih hasanil khaliƙeen”. Ta furga a saman lips ɗinta, lokacin da ta sauƙe ƙwayar idanunta kan fuskar Moddibo, da sauri ta kuma lumshe manyan Idanunta sabida wani irin masifeffen sheƙi da ta hango sajenshi dake kwance lip-lip yanayi, Sautin dariyarsa da har yanzu yake ne yasata saurin buɗe idanun. “Subahanallah, tsarki ya tabbata ga Ubangiji da ya halicci wannan bawa ya kuma bashi waɗan nan haƙoran”. Ta faɗa a fili lokacin da taga ƙyellin da haƙoransa keyi har yana ɗauke mata idanunta, Lobgoɓar da kanta tayi bisa kafaɗarta. Wani irin sassayan numfashi ta fesar tare da tsaida idanunta a kanshi. Shi kuwa Moddibo dariya yakeyi mai sayyan sauti wanda yake da daɗin ji, har maƙolloton wuyanshi yana ɗan haurawa yayi sama kana ya dawo ƙasa. Yayinda ya ɗaura tafin hannunsa kan ƙirjinsa. Cikin tsananin dariyar ya samu ya ɗan tsagaita tare da furta. “Astagfurillah watubu ilaik”. Sai kuma ya ɗago ya kalli M Jameel lokaci ɗaya kuma ya sake sakin dariya mai sauti yana cewa. “Astagafitillah Wayyo cikina”. Cikin rage girman idanunta take kallon gashin girarsa dake kwance lip. Jameel kuwa sai Murmushi yakeyi tare da girgiza kansa. Yayinda Adda Adama ma dariyar takeyi harda riƙe ciki. Ita kuwa Khausar gaba ɗaya ta kasa ɗauke idonta daga kansa. A haka har rana tayi mudun kuyanƙi alamun yana gab da faɗuwa. amma kafin ya faɗi saiya rabu kashi biyu. Yayinda Khausar kuwa ke zaune tana fuskantar yamma hakan yasata ganin abin. Atake hankalin ta ya tashi ganin yanda ranan ya rabu kashi biyu. Ita kuwa Adda Adama hannu tasa ta dafe ƙirjinta tare da faɗin. “Innalillahi wa'inna ilahi rajiu'n yau mun shiga ukun mu ku dubi yanda ranar tayi fa!”. Tana faɗin haka duk dariya da murmushin da sukeyi ya tsaya. Moddibo kuwa daga inda yake zaune ya ɗaga kansa sama tare da juyawa bayanshi kana a hankali yace. “Ya Salam ya ilahi ya mujabat da'awati meke Shirin faruwa”. Cikin tsananin gigita da tashin hankali da firgici Khausar ɗin ta saki kuka mai cike da rauni tare da cewa. “Innalillahi wa innailaihi raji'un, hasbunallahiwani'imanwakil, mun shiga uku”. Sai kuma ta juyo ta kalli Moddibo da ya gyara zamanshi kana a hankali yace. “Babu abinda zai faru wanda Allah bai sani ba, Insha Allah Ubangiji zai mana maganin duk kan abinda yayi tsanani”. M Jameel kuwa kasa furta komai yayi sai hawaye dake kwaranya daga idanunsa. ita kuwa Khausar ganin M Jameel na Hawaye kawai sai itama tashiga yin kuka amma ba mai sauti ba. Cikin wani irin yanayin da bazai misaltuba Moddibo ya dubesa kafin yace. “Haba J. Kamar ba namiji ba addu'a ya kamata muyi duk kan tsanani yana tare da sauƙi”. Still dai M Jameel baice komai ba. Shi kuwa Moddibo cikin sanyin jiki ya fuskanci Khausar cikin wata iriyar murya yace. “Khausar tausayi na kike ji ne?”. Cikin kwaranyar hawaye ta gyaɗa mishi kai tare da sakin raunataccen kuka mai cushe numfashi, lokaci ɗaya numfashin ta ya fara cushewa yana ɗauke wa, cikin yanayi wahalar neman numfashi taga Moddibo ya...! Dai-dai lokacin kuwa ta farka daga baccin da takeyi ciki razana tare da kaɗuwa ta dafe kanta da takeji yana jujjuyawa. Kana duk da sanyi da ake tsulawa a garin wani irin zufane ke tsastsafo mata ta ko ina. Cikin sauƙe ajiyar zuciya, ta juya gefen hagunta ta karanta A'uziyya ƙafa uku kana ta canza hannun kwanciyar ta zuwa dama. Sai dai sam baccin yaƙi zuwa mata, sai ta kama karatun Alqur'ani cikin sassayan sauti, Cikin ikon Allah ta samu bacci ya kuma yin awon gaba da ita. Baki ɗaya Wunin wannan ranan akasalance tayi koda abinci ta kasa ci haka zalika koda yawan surutu sai ta rage sosai mafarkin ya tsaya mata arai da zaran ta tuna irin mafarkin da tayi sai taji zuciyarta ta buga da ƙarfin gaske. Da daddare cikin ikon Allah data karanta Alkur'ani mai girma tare da bin haddarta da Malam Liman ya bata sai taji sauƙin abin aranta duk da kuwa bawai ta daina jin tsinkewar zuciyar bane amma ya ragu sosai. Da misalin ƙarfe takwas da rabi na dare Khausar suna zaune a farfajiya gidan Hajja Nana su uku ita Yaya Abba da kuma Dije suna hira jefi-jefi take sanya musu baki aciki daga ƙarshe ma ta miƙe tace zata je ta kwanta sai Dije ma ta miƙe ganin haka yasa Yaya Abba ya musu rakiya har gida. Washe gari:Da safe still haka Khausar ta tashi bata da wani ku zari koda abinci ne ta kasa ci iyakacinta tasha Tea ko ruwan kunu sannan ta kasa faɗawa kowa irin mafarkin da tayi domin jikinta ya mutu sosai da mafarkin. Da daddare ba kinta ɗauke da Sallama tashiga gidan Hajja Nana. Asaman laɓɓa Hajja Nana ta amsa mata Sallamar tana binta da harara dan tunda taƙi markaɗa mata wake take jin haushi ta. Ita kuwa khausar bata masan Hajja Nana nayi ba ta nemi waje ta zauna tare da kallon Hajja Nana tace. “Yunwa nakeji ki bani abinci zanci”. ta faɗa tana kallon ƙorenta dake jere guda goma sha Uku. Harara Hajja Nana ta wurga mata tace. “Gashi ki ɗauka ki ci”. Kai Khausar ta gyaɗa tare da Matsawa jikin ƙoren tashiga buɗewa ɗaya bayan ɗaya tana dubawa saboda taga gidan Malam Liman anyanka kaji cikin Sa'a kuwa tana buɗe ɗayan taga Jan miyar dage-dage da kuma tuƙeƙƙen tuwon shinkafa. Ta gyara zamanta tare da wanke hannunta ta fara cin tuwon cikin Mintuna kaɗan ta cinye tass sannan ta kuma janyo wani Ƙoren dan sosai take jin yunwa sannan bata wasa da cikinta dan ita dai ko ciwo bai cika hanata cin abinciba karo na forko kenan a rayuwarta da abu ya tsaya mata a rai har ya hanata cin abinci na kwana biyu son ta Tara yunwar shiyasa. ta cinye ƙore biyun tas dan dama tuwon ba wani mai yawa ake samata ba tunda akwai yawan kanukan. Hajja Nana kuwa juyawa tayi da mamaki ta kalleta kafin tace. “Yanzu har kin cinye tuwon nan”. Kai Khausar ta gyaɗa mata tace. “Na cinye mana kuma yanzu ma ƙarawa zanyi dan yunwa nakeji rabo na da abinci tun shekaran jiya da daddare fa sai dai in ta Shan abu mai ruwa-ruwa”. Taɓe baki Hajja Nana ta kuma yi tace. “Toh bubbuga rumbu ga shican ki ƙara ki cinye duka ma in Kinga dama”. Ta Faɗa tare da tura mata wani akoshin. Ɗauka Khausar tayi kamar wasa ta cinye dake abincin ba wani da yawa ake sawa aƙoron ba dake sun san cewa ƙorenta da yawa mafi yawan lokuta ma loma ɗaɗɗaya takeyi ako wani ƙoren idan tayi loma sha uku ya wadatar mata a dai cikin tsohuwa ta kuma tsinci nama ta cinye to shiyasa ba'asa mai yawa. Ita kuwa Hajja Nana ganin yanda Khausar ke cin abinci yasa tayi zaton gatse take mata ta harareta da faɗin. “Mutum kamar jaki wannan ci haka ki cinye wannan ƙoren ki cinye wancan”. Ta ida maganar tare da sake tura mata wani ƙoren. Ita kuwa khausar ta ƙoshi amma saboda ta ƙular da ita yasa ta janyo ta buɗe naman kan abincin ta cinye sannan ta gutsiri kamar loma biyar ta zuba akwanan dake empty. Wani kwanon Hajja Nana ta kuma tura mata still ta cinye naman ta kuma gutsura ta zuba a sauran kwanon. Hajja Nana ta dube ta cikin tsareta da ido tace. “Wai har yanzu baki ƙoshi ba?”. Khausar cikin yamutsa fuska ta gyaɗa kai kana tace. “Eyyy ban ƙoshi ba”. Wani akoshin Hajja Nana ta sake tura mata, Khausar kuwa laluma ta cigaba dayi idan taji da nama ta cinye ta gutsits-tsira tuwon ta bari. Ita kuwa Hajja Nana kamar wacce akace ta leƙa taga aika-aikan da Khausar keyi da tuwon ta miƙe cikin fushi tace. “Shegiyar yarinya gantalelliya ni kike nunawa barikanci, 'yar banza kinje kin zauna gidan Mayu kema kin koma kamar Mayya, sai cin nama kamar kura, wato ma duk naman kike lalubewa dan mayta ai dai na sani in dai ba cikin zanine da keba ai yaci ki ƙoshi”. Ya mutsa fuska Khausar tayi tare da riƙe ƙugunta tace. “Naci ɗin idan ni Mayya ce kinsan inda na samu maita, tunda nazo saboda shegen maƙo ko zabuwa ɗaya kin kasa yanka min gaki da Zabbi kamar zasu kashe ki ga shanu kuma aina Babana ne”. Salati Hajja Nana tayi tare da fashewa da kuka. Kasancewar duk dare aƙofar gidan ta suke zama yasa Baffa Umaru daya ji sautin kukan ta ya miƙe kasancewar Allah ya bashi kunne komai ƙanƙantar sautin abu ya kan iya ji. Ganin Hajja Nana na kuka yasa Baffa Umaru nufarta tare da cewa. “Addah Nana Meya faru?”. Nuna Khausar tayi da hannu kana tace. “Wannan ‘yar Usmanu har zata min gori wai gadon Ubanta na riƙe kaji shegiyar gantalalla yarinya dan ma Allah yayi dan ke macece!” Ƙasa da murya Baffa Umaru yayi yace. “Dan Allah Addah Nana kiyi haƙuri kinsan yarinta ke damunta idan ta girma ba zatayi ba”. Ya ida maganar tare da jan hannun Khausar suka fice waje. Bayan sun fita ya juya ya kalleta yace. “Haba Khausar kidena ki koyi yanda zaki zauna da manya kinga Addah Nana tsufa ya kamata tana buƙatar rarrashi da lallami, kinga duniyar nan ba matabbata bace idan yau kaine gobe ba kai bane ita rayuwar nan bata da tabbas, ki koyi magana mai daɗi ke idan Mahaifinki ina ita fa ɗan ta ne data haifa acikinta kuma ɗan ta mafi soyuwa agareta kada ki sake haka kinji Khausar am”. Ta gyaɗa masa kai da faɗin. “Toh shikenan Insha Allah bazan sake ba”. Ya shafa kanta yana murmushi yace. “Allah ya miki albarka kizo muje gidana mu kwana zansa ayanka miki Zabbi kici tun da mun gama cin abinci". Kai ta gyaɗa tare da yin murmushi tace. “Toh”. Ya riƙe Hannunta suka tafi suna tafiya suna hira har suka isa gidan bakinsu ɗauke da Sallama suka shiga gidan Adda Adama ta fito daga ɗaki tare da amsa musu sallamar. Kallon Adama Baffa Umaru yayi yace. “Akwai nama ne?” Adama tace. “Eh akwai Zabbin da aka yanka da yamma yanzu nake ƙarasa dahuwarsu”. Yace. “Toh shikenan ki ƙara sa gyarasu ki kawo ma wannan Kuran Birnin taci”. Dariya Khausar tayi tana zama akan taburman da Adama ta shimfiɗa musu, shi kuma Baffa Umaru ya zauna daga gefenta yayin da Adama taje taci gaba da aikinta kasancewar farin wata ya haska ilahirin garin. Anutse Baffa Umaru ya kira sunanta da faɗin. “Khausar”. Ta ɗago kanta tana kallon fuskarsa acikin farin watan kafin tace. “Na'am”. Idanunsa kanta yace. “Kinsan kamannin Babanki?”. Kai ta girgiza masa tare da faɗin. “A'a bansan kamanninsa ba”. A sanyaye yace. “Amma kin san akwai Baffanki ai yayan Babanki Hammadu Ɓadamaya ko?”. Tace. “Eh amma Ɓadamaya yake ko?”. Yace da ita. “Eh yana can Ɓadamaya dashi da Iyalansa da kuma ahalinsa gaba ɗaya. Insha Allah wataran Zakije shida Babanki Uwa ɗaya Uba ɗaya". Kai ta jinjina da faɗin. “Eh Mommy na tafaɗa min cewa inada Baffa yana can Ɓadamaya dashi da matarsa da kuma ‘Ya‘yansa”. Murmushi yayi yace. “Toh idan kinje zaki ga mai kamannin Mahaifinki sak da sakin sunan sa Aliyu shine yake kama da Mahaifinki ya gaji Babanki komai da komai kuma shine aka aurawa yayarki Nenne”. Kai ta gyaɗa tace. “Toh yaushe zanje in gansa?” Yace. “Kinga kamannin Mahaifinki kamar balarabe kinga ba yabon kai ba mutanen Rugar mu duka kyawawa ne amma kyawun mahaifin ki ya fita da ban farin Mutum ne kyakkyawa ga kuma gashin kansa mai tsawo da sheƙi wannan gashin naki ma shi kika ɗauka”. Idanunta ta lumshe cike da kewar mahaifinta sai kuma ta buɗe su tace. “Aikam nasan gashin sa na ɗauka ba Mamansa ba da kai agwagwiye". Murmushinsa ya faɗaɗa da faɗin. “Ina Addar tawa kike yiwa ba'a itama tsufa ce yasa gashinta kaɗewa”. Murmushi tayi tace. “Ai lalle kam”. Sai kuma ta dai-dai-ta nutsuwarta tace. “Ku kuma dama nan ne asalin Rugarku?”. Kai ya gyaɗa mata yace. “Eh asali nan ne Rugar mu iyaye da kakanni”. Tace. “Toh Meyesa ita Hajja Nana ta dawo nan kuma ina ne asalin garinsu Babanmu?” Murmushi yayi yace. “Asalin garinsu Babanki yana da nisa lokacin da Addarmu tayi aure ta daɗe kafin tazo ta samu haihuwa to data haifi na farko sai Allah ya sake kawo wasu akan lokaci ta haifi yara uku sai Allah yayiwa kakanki daya haifi Babanki rasuwa,sai ta nemi zata dawo to data nemi zata dawo sai sukace tabarmu su yaran ita kuma tana son yaran sosai sai tace Inde akan dukiya ne tabar musu duka subarta ta taho da ‘Ya‘yanta”. Zama Khausar ta gyara tana sauransa da kyau. Shi ko a hankali ya cigaba da cewa. “Dake dangin Mahaifinki mutane ne masu karamci sai sukace su ba dukiyar su suke buƙatar ba kawai dai suna so suriƙa ganin ɗan uwansu ne sannan ita macece kada subar mata nauyi amma tunda tana son Zama da ‘ya’yanta baza su hanata ba sai suka bata duka gadon Mahaifinki da kuma na Baffanki da ƙannensa mata biyu hadda mai sunanki. A ranar da tashigo Rugar nan tashigo da aƙalla shanu sun kai ɗari biyu sannan harda raƙuma da tumakai duk gadon sune aka ɗauka aka basu suka dawo”. Sassayan ajiyar zuciya ta saki tana jinjinawa lamarin. Baffa Umaru ya cigaba da cewa. “Toh tun daga lokacin ne zamanta ya dawo nan daga baya Allah yayiwa mahaifan mu rasuwa da gida huɗu ne kacal anan mahaifinmu su suka fara kafata da duk nan dajine mahaifinmu ne ya sare bayan rasuwar mahaifinmu da kuma mahaifiyarmu, itace ta zame mana Uwa da uba tun muna yara itace ta renemu nida Mahaifinki mun taso tare atare mukayi wasan ƙasa ta raine mu tare ta zame mana kamar uwa Shiyasa mu awajen mu Adda Nana ba ya bace kaɗai uwa ace a garemu”. Ita kuwa khausar Ajiyar zuciya ta kuma saki tare da faɗin. “Ikon Allah Allah mai iko Mabuwayi Gagara misali”. Murmushi Baffa Umaru yayi yace. “Kin gane ko mu Addah Nana Uwace agaremu ba Ya ba sannan maganarta Umarni ne awajenmu muda ‘Ya’yanmu babu mai saɓa mata har jikokin mu kinga keda kika zo kina wannan abin sai akaga lallai ta samu karan tsaye”. Murmushi Khausar tayi tace. “Lallai dai kam,to amma ina ne asalin su Babanmu?”. Murmushi yayi yace. Gobe zan faɗa Miki Idan Allah yakaimu rai da Lafiya zan ƙara sa baki labarin insha Allahu”. “Toh Allah ya kaimu goben lafiya”. Cewar Khausar Cikin sauƙe numfashi yace. “Naji ma Addah Nana na cewa kafin ki koma Abbah zai kaiki Ɓadamaya kije kiga Baffanki da ‘Ya‘yansa”. “Toh ina kuma ance da nisa?”. Khausar ta tambaya “Eh danisa amma ai tafiyar wuni ɗaya ce zaku isa”. Ya bata amsa. Miƙe sawunta tayi bisa taburmar tare da cewa. “Toh shikenan ba matsala, Insha Allahu zamuje, nima ingansa sannan kodan inga mai kama da Babana”. Murmushi yayi tare da cewa. “Sannan kuma kafin ku tafi zakuje kiga Addarki ‘yar Baffanki da yake Ɓadamaya tana nan Rugar Fulani dake ma ƙobtanmu Adda Ikki aikin santa?”. Murmushi tayi tare da gyaɗa masa kai tace. “Eh na santa ai itakam tana zuwa har gidanmu ta dubani duk dangin Babana ma ita nafi sani”. Yace. “Toh shikenan Zakije wajenta kiyi kwana biyu”. Tace. “Tun kwanaki nake cewa Hajja Nana zanje in dubata, tace min ba yanzu ba, wai in bari ingama sanin mutanen garin nan”. Adama dake sauraron hiransu ta miƙe hannunta riƙe da kwanan da ta gama gashin Zabbin dake ta tashin ƙamshi sannan ta haɗo musu da madara mai ɗumi. Akan tabarmu ta ajiye musu su duka ukun atare sukaci. Gyatsa mai sanyi Khausar kana tace. “Kai gaskiya naci naji daɗi Nagode”. Bayan sun kammala ne Khausar tashiga ɗakin Adama ta kwanta Adama kuwa ta nufi ɗakin mijinta suka kwanta tare. Can cikin dare kamar misalin ƙarfe biyu Baffa Umaru ya miƙe zaune, tare da kasa kunnensa sosai wanda hakan ya kasance ɗabi'arsa ne, domin shine Garkuwar Rugar tasu, jin motsin tashin sa yasa Adama miƙewa ita ma ta zauna, kusa dashi tana faɗin. “Lafiya”. Ajiyar zuciya ya saki da faɗin. “Naji tsayuwar mota daga can nesa sannan naga haske yashigo har cikin garin nan kamar da akwai wani abu ko dai munyi baƙi ko kuma wani abu!". Ahankali tace. “Toh yanzu fita zakayi kenan?”. “Dole in fita ai Adama idan ban fita ba ‘yan uwana zan bari wani abu yazo ya ritsa da mune ai bazan bari ba dole in fita inga ko menene”. Ya faɗa a hankali. Ita kuwa Adama riƙe hannunsa tayi fuskarta na bayyanar da tashin hankali tace. “Nikam ina tsoro wallahi”. Da sauri yace. “Kada ki damu Insha Allah babu abinda zai faru wanda Ubangijin bai sani ba”. Kai ta girgiza kana tace. “Kai rashin network ɗin garin nan yana damun mu wallahi, kaga da akwai network tunda yawanci kowa yana da waya zaka kik kira su awaya kowa ya fito kaga idan yaso sai sufito ku haɗu Atsakiyar garin amma Ni ina tsoron fitarka kai kaɗai”. Suna cikin Maganar ne sukaji antura ƙofar gidansu anshigo Murfin ya fadi ƙasa Kifff kasancewar ba wani Murfin kirki bane gadon kara ne da gwafa aka haɗa. Cikin han zari ya mike ya tsaya. Itama miƙewa tayi da saurin ta riƙe hannunsa tace. “Fita zakayi dan Allah kada ka fita ka tsaya dan Allah kar ka fita”. Ya juya ya fuskanceta yace. “Ya kike so inyi idan ban fita ba kina jifa anshigo gidan nan”. Yana ida maganar ya fin cike hannunta dake cikin nasa ya fita. Cikin sauri ta shari gabansa ta fito ya zama na itace agaba shi yana bayanta. Suna fitowa idanunsu ya sauƙa akan mutanen uku dake sanye cikin baƙaƙen kaya hannunsu riƙe da bindigi da kuma toch ligh mai masifar haske. Arazane Adama tace. “Innalillahi wa'inna ilahi rajiu'n Hasbunallahu wani'imal wakin”. Ƙaran buɗe ƙofa da kuma sautin Muryan Adama ne ya fito da Khausar daga ɗaki wacce farkawanta babu daɗewa tana fitowa sukayi saurin kashe mata ido da hasken toch ligh dinsu ita da Adama. Cikin daga Murya suka ce da Adama “Ki matsa agabansa kada jini ya taɓa ki ki matsa kada mu illataki!”. Aruɗe tace. “In matsa agabansa!?Bazan matsa ba, ku suwaye ne? sannan me kuke nema? me kuka zo yimana acikin daren nan?”. Ɗaya daga cikin sune yace. “Kashe sa muka zo yi!”.. Cikin tsananin tashin hankali tace. “Innalillahi wa'inna ilahi rajiu'n hasbunallahiwani'imanwakil. dan Allah kada ku kashesa,me yayi muku zaku kashe sa?,Meyesa?”. Ɗaya daga cikinsu ba wanda yayi magana da farko ba yace. “Saboda yana hanamu rawan gaban hantsi zamu kashe sa muga takan tsiya bashi yace taurin kai ba”. Baffa Umaru kuwa murmushi yayi mai cike da Jarumtaka da kuma rashin tsoro yace. “Ni zaku kashe?,To idan kunga na mutu kwana nane ya ƙare,Kuma Ubangiji shi ya ɗauki raina. Amma ku baku isa ba babu mai rayawa babu mai kashewa sai ubangiji. Dan haka raina baya hannunku kuma ajalina baya hannunku idan kunga na mutu ma kada kusa aranku ku kuka kashe ni!”. Ya ida maganar tare da zabura zai shiga ɗaki dan ɗauko kwari da bakasan. Ita kuma Adam da saurin riƙesa dai-dai lokacin da suka harbesa akafaɗarsa na dama. Ƙaran harbin ne ya tashi gaba ɗaya ilahirin mutanen garin Aɓangaren Hajja Nana kuwa tana tashi daga bacci sanadiyyar ƙaran harbin ta dafe kanta da faɗin. “Wayyo Umaru na Allah ka kare mana Umaru” domin shine mutum na farko daya faɗo mata arai cikin rawan jiki ta miƙe tare da ɗaukar zaninta ta ɗaura kana ta ɗauki mayani ta yana. Aɓangaren Baffa Jauro yana miƙewa yace. “Umaru”. Ya kira sunan sa cikin daga murya. Baki ɗaya ‘Yan uwansu da sauran jama'a babu wanda ya faɗo masu arai sai Baffa Umaru ko wannensu daya farka zai ce. “Wayyo! Umarunmu”. Shi kuwa Umaru juyawan da zai yi sai suka samu damar sake harbinsa ahaƙarƙarinsa na hagu. Cikin ƙarfin hali da ɗaga sautin Muryar sa yace. “La'ilah ha Illallahu Muhammad Rasulullahi(S.A.W) Adda Nana ki yafemin yau kam zasu kashe ni ki yafemin kece madadin Uwa awajena duk abinda nayi ki yafemin yau kam sun kasheni sun kashe ni,Yaya Jauro, Yaya Sadu, Yaya, GarGa, Yaya Liman, Yaya Garba,Yaya Sale yau kam sun kasheni sun cire muku ɗaya cikin goma kun zama ku tara!”. Adama kuwa Aruɗe ta riƙesa jikinta na kyarma taja numfashi amma ta gagara sakewa. Ita kuwa Khausar numfashin taja amma ta gagara sakewa saboda tsananin ruɗu da tashin hankali da tashiga kamar zata shiɗe!. Ihun da kiran sunan da yake yasa suka janye toch ligh ɗin su dake fuskar Khausar da Adama suka mai dashi sama wannan dalili ya bawa Khausar damar kallon fuskokinsu da kyau amma baki ɗaya jikinta ya sandare bata da wani kataɓus ɗin motsawa. Su kuwa ƙirjinsa suka saita suka sake harbinsa akwai wani ƙaton tukunya agefen ya ratsa ya ɓula. Shi kuwa Baffa Umaru ƙirjinsa ya dafe da faɗin. “Laila Ha'illalhu Muhammad Rasulullahi (S.A.W)” Shikenan rai yayi halinsa. Su kuwa mutanen garin baki ɗaya gidan Baffa Umaru suka nufo ko wannensu na rataye da kwari da bakansa sukuwa jin hayaniyar mutanen yasa suka ɓulla ta bayan gidansa suka fice tare da zuwa inda suka bar motarsu suka shiga. Shi kuwa Baffa Umaru ta cikin tukunyar gefensa ya faɗa jini nata ɓulɓula. Hajja Nana ce farkon shigowa yayin da gaba ɗaya ilahirin jikinta ke rawa tana isa tsakiyar gidan, Ƙofar dakinsa ta nufa, tana isa inda yake ta janyo gawar ta rungume tana kuka tare da faɗin. “Umaru! Umaru!! Umaru!!! Yau kuma mai zan gani gawar Umaru zan riƙe ahannuna kamar yanda na riƙe gawar Usmanuna!”.Cikin kuka sosai take maganar. Su Baffa Jauro da sauran mutanen ne suka shigo sudai Allah Allah suke su ƙarasa cikin gidan suga abinda ya faru dashi sam basu yi tunanin bin bayan mutanen ba. Ita kuwa khausar hanyar da suka bi suka fita take nuna musu da yatsa ta kasa furta komai bare kuma ta taɓuka wani abun Yaya Abba ne da ya shigo yace. “Yayane Khausar!?”. Cikin matsananci kuka da tashin hankali tace. “Yaya Abba sun gudu sun kashe shi sun gudu sunbi ta nan na gansu sunbi tanan!”. Azabure Matasan suka bi wajen ina tuni sun shiga motarsu sun gudu sukuma su Baffa Jauro, Baffa, Sadu da sauran rungume gawar ƙaninsu sukayi suna kuka. Hajja Nana kuwa tattaɓa jikinsa tayi, Sadik yace. “Baba mu ɗaukesa mu kaisa asibiti”. Sake rungume gawarsa Hajja Nana tayi tace. “Saddiƙu wani asibiti zamu kaisa bayan sun kashe sa baya numfashi bashi da rai!?”. Jauro ne ya karɓesa ya duba shima ya rungumesa ganin ya rasu Baki ɗayan su akan Gawarsa suka kwana. Ita kuwa khausar gaba ɗaya ta rikice ta duburburce bata taɓa gani ankashe mutum agaban ta ba sai lokacin tayi kuka har ta godewa Allah manyan Idanunta sunyi luhu-luhu dasu ba abinda ke faɗo mata arai kamar yanda sukayi hira dashi. Washe gari akaje aka kira Ƴan sanda acikin gari suka je sukayi bin cike tare da rubuce-rubucen su na banza da wofi sannan akayi masa sallah aka kaisa gidan sa na gaskiya. Kana akazo aka zauna zaman makoki, Addar Khausar Ikki da zata je wajenta a Rugar Fulani ce tazo da taji labarin rasuwar Baffa Umaru tana zuwa kai tsaye gidan Baffan Umaru ta nufa duk ‘yan uwan suna can suna karɓan gaisuwa. Khausar na ganinta ta tashi da gudu ta Rungumeta tana kuka tace. “Addah Ikki agaba na agabana fa suka kashe shi sun harbesa sun kashe sa ya rasu har lahira!”. Addah Ikki tace. Kiyi shiru Khausar duk mai rai mamacine addu'ar mu yake buƙata”. Kai Khausar ta gyaɗa amma ta gaza tsaida kukan ta Ganin haka yasa Addah Ikki taja hannunta suka fita zuwa gidan Hajja Nana. Suna Shiga Khausar ta tsaya cikin Muryanta daya dishe da kuka tace. “Ni ina tsoro bazan shiga ɗakinta ba akwai kuliya”. Addah Ikki tace to kitsaya na koreta sannan tashiga ɗakin ta fito da kuliyar tasa awani ɗaki ta rufe. Sai asannan Khausar ta yarda tashiga ɗakin bayan sun zauna Addah Ikki ta zauna ta riƙa yi mata nasiyya tare da kwantar mata da hankali. Yaya Abba ne ya ɗauki wayarsa ya tafi Bishiyar ƙare zancenka ya kira duk dangi na nesa ya riƙa sanar da su har ya kira Baffa Hammadu na Ɓadamaya ya sanar masa. Shima washe gari Baffa Hammadu ya ɗauko iyalansa baki ɗaya suka taho da yammaci gab maghariba motocinsi su guda biyu ajere suka shigo Rugar kai tsaye ƙofar Hajja Nana suka nufa sukayi parking motocinsu. Ita kuwa Khausar na cikin ɗakin Hajja Nana manne da jikin Addarta Ikki suka jiyo Sallama, Addah Ikki ce ta miƙe da faɗin. “Laaa Umma na sannan sai Baffanta yashigo daga bayansa kuma wani kyakkyawan matsakaici mutun ne fari ƙal kamar balarabe yayin da Yaya Abba ke biye dasu abaya. Durƙusawa Khausar tayi tare da fashewa da kuka kalaman Baffa Umaru ne kawai keyi mata suwwa akunne. Rarrashinta Addah Ikki ta shiga yi tana bata haƙuri da kyar ta tsaida kukan tace. “Addah Jiya da daddare Baffa Umaru kece min Baffana na Ɓadamaya yana da wani ɗan sa dake tsananin kama da Babana Addah Ikki wannan shine ke kama da Babana?”. Cikin matsanancin kuka ta ida maganar. Kai Addah Ikki ta gyaɗa mata alamar Eh. Ita kuwa khausar kanta ta kife acinyar Addah Ikki ta cigaba da rera kukanta. Baffan Hammadu ne ya riƙe hannunta ya cewa. “Khausar kiyi shiru kada kiyi kukan rashin Uba nima Mahaifine agareki ni zan tsaya Miki madadin Uba ako ina dan dai Banason rabaki da mahaifiyar kice Shiyasa na barki kike zaune tare da ita muddin ina raye zan maye Miki gurbin Uba”. Cikin raunin murya tace. “ Baffa Allah hokke sabbugo”. Ameen thumma ameen suka amsa.k Kana suka tafi gida Baffa Umarun. Bayan angama zaman Makoki Khausar tabi Addarta Ikki can Rugar Fulani tayi kwana biyu sannan suka dawo bayan sun dawo akayi addu'ar bakwai Baffanta na Ɓadamaya yafara shirin tafiya sai asannan Khausar taga sauran ‘ya‘yan sa daya zo dasu harda Mata bayan sun sake ganawa ne suka tafi. Akwana atashi ba wuya Khausar ta cika Makwanni uku Arugar Jauro yaya yayin da Baffa Umaru keda mako biyu da rasuwa kullum ‘Yan uwansa matarsa kuma jama'ar gari cikin yi masa addu'a suke domin baza su taɓa mantawa dashi atarihin rayuwarsu ba da kuma irin gwagwarmayar da yayi adomin kare rayukansu. GEMBILA Acan ɓangare makarantarsu Khausar kuwa ayaune aka gama gyara ilahirin makarantar daga nesa idan ka hango ginin ba zakayi zaton cewa a Gembila makarantar take ba koda a ƙasashen turawa ne sai ’Ya’yan wane da wane saboda yanda aka ƙawata ginin Makarantar fentin ya kasance Maroon and White haka zalika gate din Maroon anda white ne daga sama An rubuta *Al'ANSAR ACADEMIC SCHOOL* Rubutun ma Maroon and White ne. Acikin harabar makarantar kuwa Moddibo ne tsaye hannunsa harɗe aƙirji ya yinda manyan idanunsa ke lumshe yana kallon tsarin ginin Makarantar da akayi wani irin Up stair cycle daga cikin harabar makarantar zagaye yake flowers masu kyau da tsari. M Jameel ne yace. “Gaskiya Moddibo kayi ƙoƙari makarantar yayi masifan tsaruwa”. Murmushin gefen baki Moddibo yayi wanda ke ƙarawa fuskarsa kyau yace. “Masha Allah haka akeso”. Ya ida maganar tare da juyewa cikin nutsuwarsa yake tafiya har suka fita acikin harabar makarantar suka shiga motarsu dake gefe afake. Moddibo ke Driving yayin da M Jameel ke gefen mai zaman banza ƙira'an Sudai's na tashi cikin suratul Nisi'i Moddibo kuwa jinjina kai yayi ayoyin na ratsa sa. M Jameel ya juya ya kalli Moddibo da bakinsa ke motsi alamar karatun yake bi yace. “Moddibo kamar akwai motar dake bin mu fa”. Kai Moddibo ya girgiza yace. “A'a ba binmu akeyi ba”. Kai M Jameel ya gyaɗa still yana kallon mirror bai dai ce komai. Daga nan suka ci gaba da tafiya ganin still kamar binsu akeyi yasa Moddibo ya tsaya. Ga mamakin su ganin su tsaya yasa wancan motar tayo kansu gadan-gadan...! *Wasan fa yanzu aka farashi. Bakin zaren labarin sun kai 12 dozi. Kenan. Akwai ababen dake a duhu fa. Saninsu sai kun bibiyu Al'ƙalamin Shatu yar Aliyu Garkuwa. Jikar Muhammad Babayo Maiturare. Kana kuma (BODDIN DEDDE)* By *GARKUWAR MARUBUTA* [19/07, 7:44 PM] Halimatu A/rahman Sadeeya: 📝🍇✨💫⏰🤴🏻👹❤️❤️❤️🍇 *SAKAYYAH* _Page 8_ _NA_ *AYSHA ALIYU GARKUWA* 🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 *Free page ne ƴar uwa in sun ƙare ko kinga littafin SAKAYYAH a a waje ba a cikin Groups na na SAKAYYAH ɗin da nabuɗeba, toh na satane kuma na Allah ya isane, kana na Yaseen doguwane😂 bulluƙutu kuma baƙar mutuwa... Dan haka biya ki karanta cikin Salamah yar uwa ba haƙƙin kowa kanki, littafin SAKAYYAH 1k ne kacal 0661110170 GTBank AISHA ALIYU GARKUWA sai ki turo min shaidar biyanki ta WHATSAPP 09097853276. Sai in saki a Group ki karanta abinki Nana lfy fata lfy* Masu son kayan Ɗa'a akwaisu Available. Motar tayo kansu gadan-gadan. Aruɗe M Jameel yace. “Innalillahi wa'inna ilahi rajiu'n!Hasbunallahu wani'imal wakin!! A'a su waye wannan suna da hankali kuwa!?”. Cike da al'ajabi Moddibo ya zuba musu ido tare da ƙoƙarin yiwa motar key sai kuma ya gaza yin komai ya zubawa motar ido ganin gada-gadan fa ta nufi kansu haiƙan ƙadaran. Sai da motar tazo gab dasu sai kuma ta kauce ta hau titi ta wuce. Wani irin nannauyan ajinyan zuciya mai masifan ƙarfin M Jameel ya dire tare da meda kansa ya jingina da kujerar. Shi kuwa Moddibo Idonu ya tsirawa motar cike da mamaki sai kuma ya motsa laɓɓansa a saman lips ɗinshi ya furta. “Wannan wani irin tuƙi ne?. Tuƙin ganganci ne ko kuwa dai da nufi ne?”. Dalilin da yasa ya tsaya ma atunanin sa ko ɗaya daga cikin ‘Ya‘yan Malam Arɗo ne sai kuma yaga saɓanin haka. Key yayiwa motar tare da kallon M Jameel dake lumshe da ido a hankali yace. “J nayi zaton ɗaya daga cikin ‘Ya‘yan Malam Arɗo ne ya biyo mu shiyasa na tsaya, amma inaga basu bane wata ƙil ɗan koyon tuƙi ne”. Ya ida Maganar batare daya ɗauki abin da muhimmanci ba. Kai M Jameel ya gyaɗa da faɗin. “Allah ya kyauta amma na tsorata da ganin yanda sukayo kanmu kamar da gayya suka yi sun tsinka min zuciya saura kaɗan fa su hau kanmu”. Girgiza Kai Moddibo yayi kana yace. “Da alama dai 'yan koyo ne!”. Kai M Jameel ya gyaɗa tare da gyara zamansa, kana suka cigaba da tafiya. Kai tsaye masallaci suka nufa kasancewar lokacin sallar Azahar yayi, bayan sunyi parking ne suka fito suka nufi cikin masallacin, aƙofar masallacin suka tsaya kusan tare sukay addu'ar shiga masallacin. _“Auzubillahil Azim,Wabiwajhihil Kareem,Wasulɗanihil Ƙadiym,Minal Bismillahi Wassatu Wassalamu Ala Rasulullah.Allahummaftahliy Abwabal Rahmatik”_. kana suka shiga. Bayan sun idar sun fito daga masallacin M Jameel ya juya ya kalli Moddibo yace. “Muje gida muci abinci”. Da gefen ido Moddibo ya kalleshi tare damotsa lips enshi zaiyi magana. M Jameel yayi saurin ɓata fuska tare da cewa. “Ba zakaje ba ko?”. Murmushi Moddibo yayi tare da juyawa akalar motar zuwa gidansu M Jameel. Yanzu ƙira'ar Sheykh Jabeer suke saurara har suka isa. Bayan sunyi parking suka shiga Babban falon gida Adining suka zauna sukaci abincin shikam Moddibo kaɗan yaci ya bari. Miƙewa sukayi suka fita Fitowarsu daga falon yayi dai-dai da ƙarasowar Hajiya Karima wajen M Jameel yace. “Aunty Karima ina yini”. Ba tare data amsa ba ta watsawa Moddibo kallon tsana tace. “Maƙale anzo kenan?”. Cikin ɗan sakin fuska yace. “Ehh”. Cike da mamakin halayensa da ƙarfin halinsa tace. “To wai kai dan Allah ka rabu da bawan Allah nan da dukiyar mahaifinsa mana ko zai samu yayi abin kansa!”. Cikin takaici M Jameel yace. “Dan Allah Aunty ki ƙyale Moddibo da irin wa'annan kalaman mana, na sha faɗa miki shi ba irin mutunen da kike zato bane, ta ya zan fahimtar da ke?”. Baki ta taɓe tare da juyawa tabar wajen kamar zata tashi sama. Shi kuwa Moddibo lumshe idanunsa yayi tare da cije laɓaɓɓansa na ƙasa tare da kiran sunan Allah aransa. Araunane M Jameel yace. “Dan Allah Moddibo kayi haƙuri da abinda Aunty Karima keyi maka”. Cikin kula Moddibo ya dubesa cikin yanayin nutsuwarsa da kuma ƙasaitarsa yace. “J.kada ka damu inda sabo ai yaci ace na saba da halin Aunty abinda tun tasowar mu a haka nake da ita abinda tun bamu wuce shekaru shida-shida a duniya ba take min, har yanzu da muka bawa talatin baya, ai ya zama man shafawa kawai dai abu biyu ke sawa ban taɓa yi mata wonkin babban borgoba”. Ya ƙare mgn tare da nufar ɗakin M Jameel. Cikin jinjina kai M Jameel ya bi bayansa yana mai al'ajabi abinda Modiyke ɓoyewa tsawon shekaru da yake cewa dalilin dake hanasa taka mata birki, yayi ya gaya masa kuma sam yaƙi. A ha dai suka isa, suna shiga ɗakin Moddibo ya kwanta bisa kujera tare da lumshe idanunsa alamun bacci zaiyi. Acan gidansu Lamiɗo kuwa Mommy ce zaune yayin da Asma'u ke zaune daga ƙasa gefen ƙafafunta ta ɗago kanta tace. Mommy asatin nan zamu koma makaranta gashi har yanzu Khausar bata dawo ba”. “Wallahi kuwa gashi duk kwana biyun nan ba muyi waya ba, dan munfi sati da yin mgn”. “Ayyah Allah Andi Meyesa”. Cewar Asma'u Kai Mommy ta jinjina tare da cewa. “Kuma Idan ka kiransu ba zai shiga ba sai dai idan su suka kira ka”. Gyara zama Asma'u tayi tare da cewa. “Gaskiya Mommy Idan ta kira kice ta dawo tasan ana komawa za'a fara karatu gadan-gadan”. Mommy tace. “Inasha Allah zan faɗa mata”. Daga nan sai suka ɗan ci gaba da hida, daga bisani sukayi Sallama sannan ta tafi. Acan Rugar Jauro Yaya kuwa yau sati da rasuwar Baffa Umaru baki ɗaya basu da cikakkiyar walwala duk da cewa sun dawo da sabgoginsu kamar da sai dai ciwon na nan aransu. Khausar kuwa sosai tayi sanyi tun da akayi rasuwar bata cikin hayyacinta shiyasa bata samu ta kira Mommy ta ba. Kasancewar jiya akayi adduo'ar bakwai Baffanta da yaransa duk sun koma bayan sunyi exchange na number ita dai ta Mommy ta basu. tare da yiwa Khausar al'ƙawarin kai mata ziyara wataran... Anutse Khausar ta juya ta kalli Yaya Abba cikin sanyin murya tace. “Ayyah yaya Abba dan Allah ka bani wayarka zan kira Mommy na”. Kallonta Yaya Abba yayi cike da tausayi duk tayi wata iri yace. “Toh shikenan amma ki bari sai gobe ki kirasu dan yau network bashi da kyau koda kin hau kan Bishiyar ma ba zaki ji magana ba”. Kai ta gyaɗa masa kana tace. “Toh Allah ya kaimu”. “Amin”. Ya amsa tare da miƙewa ya fita. *GEMBILA* Washe gari da safe tunda gari ya waye Malam Arɗo ke ta kiran wayar Moddibo awaya amma ba'a ɗagawa. Shi kuwa Moddibo Anutse ya farka daga baccin daya koma tare da furta. _“Alhamdulillahil Lazi ahyana bada amatana wa'ilaihil nushur”_ Wayarsa dake gefe ya janyo ganin Miss call ɗin malam Arɗo bar katai da yayi ne ya sashi ajiye wayar. Kana ya miƙe ya shiga toilet. Tare da addu'a a baki nai Wanka yayi wanda ya ɗauke sa kimanin minti talatin kana ya fito yana mai faɗin. _“Gufranaka”_ Suman kansa yake tsanewa da baby pink towel mai taushi. Yayinda yake sanye da jibgegiyar bathrobe pink color mai masifar taushi wacce ya saƙale igiyoyinta a ƙugunsa. A hankali ya zauna agaban dressing mirrow tare da, Jona handdryer kana ya kunna tare da gyara zamansa da kyau bisa kujerar, dressing mirror ɗin tare da fara busar da sumar kansa mai ɗan karen sulɓi. 56 seconds yayi zuwa 1 minute yayi yana jujjuya kan handdryer ɗin tare da sa hannunsa ɗaya dake riƙe da madaidaicin Kum. A hankali ya ajiye dryer din tare, da buɗe wani gora mai haɗe da man gashi na musamman, wanda Ummi ce ke haɗa musu, ɗan tsiyaya yayi kana ya murza tafin hannunsa tare da shafa. Wani irin sheƙi da ƙyalli mai ɗaukan ido suman nasa ya farayi tare da fidda wani ni'imtaccen ƙamshi. wani ƙum mai laushi wanda yafi na farin ya ɗauka tare da bin gashin nasa ya mishi tafiyar tsutsa, Wow masha Allah, kamar saƙan taburma haka gashin ya kwanta da salo mai burgewa. Goge tafin hannunsa yayi da towel ɗin dake bisa ƙafaɗarsa, kanaya lakato lotion ɗin sa mai daɗin ƙamshi ya shafa jikinsa baki ɗaya. idonsa ya lumshe tare da kauda kansa lokacin da yake shafawa cinyoyinsa mayin, fuskarsa ya ɗan shafawa, mai ɗin tare da sa yatsarsa babba ya kwantar da gashin giransa na gefen dama, kana yasa babbar yatsar na hagu ya kwantar da na gefen hagun. sannan ya ɗan tsiyayi man kanshin ya shafawa tattausan sajensa dake kwance lip-lip ya shafa, wani irin sheƙi sajen keyi yana fitar da sanyayyan ƙamshi. Anutse ya Miƙe ya buɗe durowarsa ya ɗauki jallabiyarsa mai masifar tsada da taushi Kalar Army green, kana ya zaro tattausan boxer and singlet farare ƙal-ƙal, ɗan sunkuyawa yayi ya sanya boxer ɗin ba tare da kalli surarsa ba. Kana ya miƙa tare da dai-dai ta zaman robor a gugunsa, Bathrobe din ya kwance, kana ya saƙalashi bisa wata yar Kekkyawar masaƙali dake gefen drowersa, singlet ɗin ya saka, kana ya zira tattausar jallabiyar dake zuba sheƙi da ƙyalli wacce kai da ka gani kasan taja kuɗi. baƙin hirami ya jawo, sanya kana ya naɗe kansa da hirami tare da sako jelar ɗaurin ta gefensa na hagu tsayawa yayi agaban Dressing mirrow tare da ɗaukar kwalbar turaren mai masifar ƙamshi ya feshe ilahirin jikinsa dashi wayarsa ya ɗauka tare da sanya wa a aljihun gaban rigarsa kana ya fice. A motarsa ya shiga bayan ya buɗe gate sannan ya fice kana ya sake fitowa ya rufe gate ɗin. Aƙofar gate ɗin gidan Malam Arɗo yayi Hong mai gadi ya buɗe masa yashiga Babban gida ne sosai sai dai kallo ɗaya zaka yiwa gidan kasan mamallakin gidan mutum nai mugun maƙo da kirta babu wani fentin arziƙi ajikin ginin gidan haka zalika ginin ɗakunan single rooms ne cikin haraban gidan kuwa koda flow babu daga can kusan ƙaramin ƙofar da zai sadaka da cikin gidan rijiya ce babba anyi masa murfin ƙarfe fitowa Malam Arɗo yayi yana murmushi. Ɗan guntun Murmushin gefen baki Moddibo ya mayar masa tare da cewa. “Ina kwana Malam ɗazu ka kira ina bacci”. Ya ida maganar yana shiga ɗakin ɗaya daga cikin matan Malam Arɗo mai suna Hajiya Zainabu domin Malam Arɗo ya ɗauki Moddibo tamkar jika. Wara ido Moddibo yayi yana kallon Hajiya Zainabu yace. “Hajiya ina kujerun ɗakin? Indai ba kujera Ni gaskiya bazan zauna ba”. Sai kuma ya juya tare da kallon Malam Arɗo yace. “Malam dan Allah asamu kujeru saboda idan sukayi baƙi su samu inda zasu zauna”. Hararansa Malam Arɗo yayi tare da cewa. “Ba kai bane kake lissafin duk abinda zai cin yemin aljihu kasan yanda gyaran makarantar nan ya cinye min kuɗi kuwa?. Yanzu ma abu biyune yasa na kira ka na farko motata ta ɓaci zaka kaini Rugar Jauro yaya sannan kuma muyi magana akan ƙara kudin school fees ɗin yara dan gaskiya saina fanshe kuɗin dana kashe a school fees ɗin forko Aradun Allah. Kai Moddibo ya jujjuya tare da yar kwaffa hana yace. “Toh ba matsala ai ka'ida iyayen yara. Yau kuma mai yasami motar ta lalace ne? Ko kuma sa maine bazaka iya ba”. Yana mai laluben aljihunsa yace. “Duka biyu, ta lalacen kuma yau du-du-du da naira ashirin da biyar na tashi”. Kai Moddibo ya sunkuyar yana mai kallon wayarshi yace. “Kuma har ina Rugar Jauro Yaya yake da nisa ne!?”. Da sauri Malam Arɗo Yace. “Koma da nisa kai zaka kaini dan badan ka matsa min akan gyaran makarantar nan ba da wataƙil in canza mota kuma da ko ban canza a ai bazan rasa kuɗin da mai ba”. Murmushi Moddibo yayi kana yace. “Dama wataƙil ne Malam koba ayi gyaran makaranta ba da wuya ka canza wannan motar. Dariya Hajiya Zainabu tayi tace. “Aikam Moddibo ka faɗi gaskiya”. Anutse Moddibo yace. “Koma dai menene dan Allah Malam ayi ƙoƙari asa musu kujeru dubi fa ba laida ba Capet ba kujere ba tiles sai siminti kawai dan Allah ka daure kasamu tiles da kujeru”. Murmushi Hajiya Zainabu tayi tare da yiwa Moddibo alamar jinjina da hannu kana tace. “Allah ya maka albarka”. Tayi maganar yanda Malam Arɗo ba zai jiba. Kai Malam Arɗo ya gyaɗa da faɗin. “Naji wuce muje". Taɓe baki Moddibo yayi kana suka fita. Ɗakin Uwar gidan Malam Arɗo suka shiga mai suna Hajiya Ramatu, Kwance suka same ta akan faranda ta shimfiɗa ta burma. Gefenta Moddibo ya ɗan zauna bisa dakalin dake mazaunin Mlma Arɗo cikin mutuntaka yace. “Ina kwana Hajiya ya jikin?”. “Da sauƙi Moddibo ya ƙoƙari?”. Tace tana mai kallonsa, kauda kansa yayi tare da cewa. “Alhamdulillah”. yana miƙewa. Yace. “Ai dole ma sanyi yata kamaku ba Capet ba kujeru asanyin garin nan kam dan Allah Malam asamu kujeru inba haka ba zasu ta cutuwa sanyi zaita kamasu sannan ya batun fitar da ita wajen?”. Tsaresa da Ido Malam Arɗo yayi kafin yace. “Moddibo! Moddibo!! Moddibo Kafita idona baka iya lissafin komai ba sai lissafin yanda za'a cinye min kuɗina ko”. Shi kuwa Moddibo kai ya karya kana cikin sanyi yace. “Ai gaskiya ne Malam ita lafiyar nan dole aneme ta”. Harara ya galla masa tare da faɗin. “Ai mun gama magana da Basiru na basa kuɗin da zai isa". Shi kuwa Moddibo kai ya jinjina yace. Malam munyi magana da Basheer kuɗin ba zai isa ba Malam fita waje fa ba abune mai sauƙi ba”. Saurin Kallonsa Malam Arɗo yayi yace. “Na fahimta wato har ƙarana suke kaiwa wajenka to kaiɗin Ubana ne da zaka sani inyi!?”. Murmushin gefen baki Moddibo yayi wanda ke ƙarawa fuskarsa kyau yace. “A'a Malam niba Babanka bane ai shawara ce dai”. Shi kuwa Malam Arɗo kai ya gyaɗa yace. “Toh shikenan naji zanyi”. Sallama Moddibo yayi wa Hajiya Ramatu sannan suka wuce ɗakin Malam Arɗo. Kallon Moddibo Malam Arɗo yayi yace. “Ya batun ƙara school fees ɗin yaran nan?”. Shi ma Moddibo Kallonsa yayi kafin yace. “Malam duk gyaran makarantar nan da akayi a asusun makaranta akayi school fees ɗin yaran yayi dan angyara makaranta baya nufin sai anƙarawa ɗalibai school fees zaka kashe makarantar ida kuɗin yayi yawa”. Baki Malam Arɗo ya cuna har Moddibo ya ida magana sai kuma yace. “In kashe makaranta fa kace? Bayan na gyara makaranta sannan kuma ga lafiyayyun malamai masu ilimi yara suna samun wadataccen ilimi ko za'a samu ilimi abanza ne? zan ƙara school fees Tabbas zan ƙara”. Murmushi Moddibo yayi yace. “Toh shikenan kamar nawa za'a ƙara?". Sai asannan Malam Arɗo yayi Murmushi yace. “Za'a ƙarawa ko wani ɗalibi dubu Ashirin”. Wara ido Moddibo yayi yace. “Innalillahi gaskiya Malam yayi yawa inma za'a ƙara ya kama dole to bazai wuce aƙara dubu biyar biyar za'a ƙara shima saboda za’a ƙara sabbin malamai ne da kuma sabbin tsare-tsare”. Kai Malam Arɗo ya jinjina yace. “Toh shikenan tunda ka matsa zan barshi ahaka”. Zama Moddibo ya gyara yace. “Akwai kuma maganar tafiya musabaƙa na gasar hadda da za'ayi za'aje Noka”. Kai Malam Arɗo ya gyaɗa da faɗin. “Wannan ba matsala ashirya komai”. Murmushin gefen baki Moddibo ya kumayi idanunsa akan Malam Arɗo yace. “Eh badamuwa Malam wato tunda kasan wannan iyayen yarane zasu biya kuɗin motar da sungulla da komai”. Dariya Malam Arɗo yayi yace. “Atoh ainima dai ina ƙoƙari tunda motoci makarantar nanne ake tafiya dasu ko”. Kai Moddibo ya jinjina yace. “Ai Malam, Ƙarfe nawa zamu tafi can jauro yayan sannan mai zakaje yi?”. Cikin sanyi yace. “Wata Rugar Fulani ce amma gaskiya akwai tafiya zamu tafi da yanzu tun da kaga ƙarfe tara zuwa sha ɗaya zamu isa Insha Allah,Yawanci ina zuwa karatu can wajen wani Malam Aliyu limamin Rugar tasu sannan kuma anyi masa rasuwa shine nakeso Inje inyi masa ta'aziyya to kaga motata ta samu matsala”. Jinjina kai Moddibo yayi da faɗin. “Allah yajiƙan musulmi toh ba matsala muje tunda dama yanzu babu abinda nake yi, amma dai zamu dawo da wuri ko tunda kasan akwai ‘yan hadda?”. Kai Malam Arɗo ya gyaɗa yace. Toh ba matsala Allah dai ya kaimu lafiya”. “Amin”. Yace Sannan ya miƙe suka shiga mota suka fice kasancewar Ashirye suke. Moddibo kuwa ƙira'ar Sheykh Jabeer ya kunna suna tafiya yana saurara tare da bin bakinsa tafiya mai ɗan nisa sukayi a haka. Malam Arɗo ne ya katse shirun da faɗin. “Gaskiya wannan tsarin ginin Makarantar yayi kyau Moddibo kayi ƙoƙari”. Murmushi Moddibo yayi yace. “Uhum Masha Allah”. Haka suka cigaba da tafiya suna taɓa hira jefi-jefi wanda mafi yawan hiran Malam Arɗo keyi shi dai Moddibo daga Uhm sai um-um. Koko yace Masha Allah ko Alhamdulillah. Suna dosan Rugar Moddibo yaga wajen kamar Rafi hayaƙi na tasowa lokaci ɗaya wani irin sanyi mai ratsa jiki ya ratsa gaba ɗaya ilahirin jikinsa Atake ya lumshe idanunsa tare da cije laɓɓansa na ƙasa. Ahankali ya juya ya kalli malam Arɗo yace. “Kai Malam garin nan akwai sanyi”. Murmushi malam Arɗo yayi yace. “Sosai ma kuwa garin akwai sanyi”. Kai ya jinjina tare da jan numfashi kana ya fesar da huci mai ɗan karen ɗumi. Dai-dai lokacin yayi parking a ƙofar gidan malam liman kana yana motsa laɓɓansa alamar Tasbihi yake. “Subahanallahi”. Ya furta a hankali sabida tsarin garin yayi matuƙar ratsa shi. Yaya Abba da shigowarsa kenan ya isa garesu tare da miƙawa Moddibo hannu sukayi musabaha kana yace. “Sannun ku da zuwa fatan kunzo lafiya?” Kai Moddibo ya gyaɗa da faɗin. “Alhamdulillah". Kallon Malam Arɗo Yaya Abba yayi yace. “Tsoho mai ran ƙarfe”. Murmushi Malam Arɗo yayi da faɗin. “Ya akayi ɗan saurayi”. Cikin alamun sanayya yayi musu jagora, har cikin ɗakin Malam Liman. Cike da mutuntaka daddataku Malam Liman yake musu marhabin da zuwa. “A'a Malam Arɗo kaine tafe, sannu da zuwa, on laleko mon njabɓa ma mon laleko bagare”. Sai kuma ya juyo ya kalli Yaya Abba kana yace. “Jeka kawo musu abin taɓa wa”. Kai yaya Abba ya gyaɗa sannan ya miƙe ya shiga cikin gida. Ba jimawa ya dawo hannunsa riƙe da Akwashi guda biyu akan faranti sannan ya koma ya sake ɗauko kofi guda biyu ya buɗe akwashin daya fi girma Gashesh-shen naman ragone da aka masa gashin ruwa ruwa yayin da ɗaya akwashin ke ɗauke da madaran shanu mai ɗumi Yaya Abba yace. “Bismilla kuci”. Bai jira jin mai zasu ceba ya miƙe yabar wajen. Shi kuwa Moddibo lumshe idanunsa yayi sakamakon ƙamahin naman daya ratsa hancinsa da kuma yanda gashin yayi kyau a ido da farko baiyi niyyan ciba amma ganin yanda gidan yake atsaftace da kuma masu gidan ga wani irin ƙamshi dake tashi yasa ya fara cin naman cikin nutsuwa tare da zuba madaran sosai yaci dan baƙaramin daɗi naman yayi ba, gashi dama baiyi breakfast ba. Malam Arɗo ma sosai yaci sannan yasha madaran wanda shi kuwa kirtansa ke hamada ci sai yazo nan yake kashe tsatsan haƙoransa shiyasa ba cika fashin zuwa duk wata yana zuwa sai biyu. Bayan sun kammala ne Malam Liman yashigo ya zauna daga gefen Malam Arɗo ya bashi hannu sukayi musabaha. Malam Arɗo yace. “Fatan mun same ku lafiya ya kuma muka ji da ƙarin haƙuri?”. Kai Malam Liman gyaɗa tare da faɗin. “Hakuri mungode Allah”. Malam Arɗo yace. “Allah ya jiƙansa da rahma da kuma dukkan musulman da suka rigamu gidan gaskiya”. “Ameen ya hayyu ya ƙayyum”. ya amsa. Shima Moddibo cike da girmamawa yace. “Malam ya mukaji da haƙuri Ubangiji Allah ya jikansa da Rahman Allah ya haskaka makwancinsa”. Malam Liman ya amsa da. “Ameen”. Baffa Liman ya kalli Malam Arɗo yace. “Muje ka gaida Babbar Addarmu wacce take madadin mahaifiyarmu”. Kai Malam Arɗo ya gyaɗa kana yace. “Toh ba matsala muje”. Ya ida Maganar suna miƙewa. Baffa Liman da malam Arɗo na gaba yayin da Moddibo da yaya Abba ke bayansu Moddibo na ƙarewa yanayin garin kallon sosai garin ya burgesa ko ina ka duba tsaf-tsaf babu alamar ƙazanta ko datti. Bakinsu ɗauke da Sallama suka shiga gidan Hajja Nana lokacin tana zaune atsakar gidan kan ta burma. Baffa Liman ya kalli Hajja Nana yace. “Ga Yayana kuma ɗalibina yazo zai gaisheki”. Tace. “Ayyah sannunku da zuwa”. Sannan ta miƙe ta shimfiɗa musu darduma dake tsaf dashi babu alamar datti ajiki komai na gidanta tsaf babu datti duk da stufanta amma komai nata tsaf yake. Sosai garin da mutanen garin suka burge Moddibo komai na garin akimtse. Gaisawa sukayi da Hajja Nana sannan suka yi mata ta'aziyya madara mai ɗumi tasa aka kawo musu. Koda sukace Alhamdulillah fir tace dolefa susha ita baƙo baya zuwa wurinta ya fita baici komaiba. Madarar kawai Moddibo yasha kasancewar ya ƙoshi agidan malam Liman Aransa kuwa sai yaba karamci da dattakon mutanen yake. Aɓangaren Khausar kuwa tana can rafi tare da Dije da Sadik sunje ɗiban ƙwan Zabbi da kuma kayan lambu dake hannun Khausar bayan sun gama suka fito kallon Sadik da Dije Khausar tayi tace. “Tunda wayar yaya Abba na hannu na zanje Bishiyar ƙare zancenka in Kira Mommy na”. Kai suka gyaɗa mata da faɗin. “Muje toh”. Bayan fitowarsu daga gidan Hajja Nana Moddibo ya ciro wayarsa da niyyar kira sai yaga ba network kallon Yaya Abba yayi yace. “Baku da network ne?”. Kai Yaya Abba ya gyaɗa yace. “Eh bamu dashi amma akwai inda zaka samu idan kana da buƙata sai muje in kaika wajen akwai service ta nan nede babu”. Kai Moddibo ya gyaɗa yace. “Eh inada buƙata gaskiya muje”. Sai kuma ya juya ya kalli Malam Arɗo da Baffa Liman yace. “Bari zamuje ya rakani in sami network ina so zanyi kira”. Baffa Liman yayi Murmushi yace. “Yau ka shigo Rugar Fulanin da basu da network sai anje annema ko?”. Dan murmushin Moddibo yayi tare da shafa sajensa zuwa gyamunsa daya ƙawata kyawun fuskarsa. Malam Liman ne yace. “Abba in kunje ku karasa cikin Rafi Modibbo yayiwa Jauron garin nan ta'aziyya sannan kuce yazo munada boƙo ne”. Jinjina kai Abba yayi sannan suka fita shi kuma Malam Arɗo da Baffa Liman suka wuce can gida domin ƙara karatu. Suna fita Moddibo ya kalli Yaya Abba yace. “Kai sanyin garin kun nan yayi yawa bari na ɗauki Jacket nasa”. Ya faɗa tare da nufar motar ya buɗe ya ɗauki farin Jacket ya ɗaura akan Army green ɗin jallabiyarsa da yayi masifar yi masa kyau. Murmushi Yaya Abba yayi Aransa yana yaba baiwar kyawunsa da kuma iya Dressing ɗin sa. Ta cikin wata siririyar hanya dake ɗauke da korayen ciyayi masu kyau da ƙamshi suka ratsa. Sai wani lumshe ido Moddibo keyi yana jin kamar ya tabbata awajen saboda yanda garin ya tsaru komai nasu mai kyaune. Ta Cikin wannan Hanyar suka ɓulla har Rafi Yaya Abba nata yi masa hira shi dai daga Uhm sai Um-um saiko Masha Allah. kasancewar sa ba mutum nai me surutu ba. Suna shiga cikin Rafin Moddibo ya dunƙule hannunsa waje ɗaya jin sanyin wajen yafi na cikin garin juyawa yayi ya kalli Yaya Abba kana yace. “Muma muna da sanyi amma sanyin ku yafi namu sosai”. Kai Yaya Abba ya gyaɗa yace. “Sosai ma ai tanan kam munfi sanyi”. Jinjina kai Moddibo yayi yace. “To ku riƙa rage Bishiyoyi mana sanyin be damun ku?”. Yaya Abba yace. “Aikuwa mu munajin daɗin sanyin”. Moddibo yace. “Masha Allah”. Acan cikin rafi kuwa Sadik riƙe yake da ƙwan Zabbi mai yawa yayin da Khausar ke riƙe da ma daidaicin kwando ahannunta wanda ke ɗauke da,Inabi,Tuffa, Mangoro,Abarba,Kwakwa, Lemo,da sauran kayan itatuwa yayin da ɗaya hannunta ke riƙe da wayar Yaya Abba tana dannawa Sadik ya juya ya kalleta yace. “Khausar da kin haƙura da danna wayar nan sai mun tsallake wannan ruwan dake gudu kinga akwai duwatsu aciki”. Still hankalinta na kan wayar tace. “Kada ka damu ai ina kallo”. Kai ya gyaɗa mata sannan suka cigaba da tafiya. Yaya Abba kuwa yana ƙoƙarin karya kwanar da zai sadasu da Bishiyar ƙare zancenka ya hango Baffa Jauro acikin Rafi juyawa yayi ya kalli Moddibo yace. Gacan Baffa na Jauron garin nan da Malam yace mubiya kamasa ta'aziyya”. Kai Moddibo ya gyaɗa yace. “Toh mu ƙara sa". Kai Yaya Abba ya gyaɗa sannan suka nufi wajen Moddibo kuwa wayarsa ya ciro a aljihu yana duba ko akwai network ata wajen Dai-dai lokacin da Khausar ta iso wajen baki ɗaya hankalinta da nutsuwar ta nakan wayar tana saka number Mommy. Kallon Dije Yaya Abba yayi wacce tuni ta tsallake ƙoramar ruwan yace. “Dije har kun ɗebo ƙwoyin?”. Kai Dije ta gyaɗa masa kana tace. “Eh Ya Abba". Moddibo kuwa sam bai lura da mutum agabansa ba, ya ɗago ƙafarsa na dama zai tsallaka yashiga rafin kenan, ita kuma Khausar ta ɗago ƙafarta na hagu zata tsallaka tafita a rafin ji kake gub suka bugi juna da ƙafafunsu. Tagal-tagal Khausar tayi baya zata fadi yayin da shikuma Moddibo da ƙyar ya tsaida kansa daga faduwar da zai yi. Ita kuwa khausar Atsorace ta saki kwandon kayan Marmarin dake hannunta tare da kai hannu ta riƙe rigarsa da hannu ɗaya yayin da ɗaya hannun ke riƙe gam da wayar Yaya Abba. A kuma lokaci guda ta rumtse idanunta tare da sakin kara. Shi kuwa Moddibo cikin hanzari yakai hannu ya riƙota sai alokacin idanunsa suka sauƙa akan fuskarta ita. Ita kuwa Khausar sassayan numfashi ta fesar jin an riƙeta bata faɗiba yasa ta ɗago kan Idanunta ne suka sauƙa akan fuskar Moddibo. Lokaci ɗaya jikinta ya ɗauki rawa na tsananin tsoro da firgicin ganinsa kawai sai ta sake hannunsa tare da rintse Idanunta tayi baya zata faɗa cikin ruwan,Cikin zafin nama yasanya Lallausan tafin hannunsa ya riƙo hannunta tare da fisgota ta tsallaka sai yayi wucewarsa batare daya juya ya kalleta ba. Ita kuwa khausar banda rawa babu abinda jikinta keyi cikin rawan murya tace. Ka-ka-kayi ha-ƙuri ban gankaba shiyasa, shi kuwa Moddibo ko juyawa baiyi ba bare yaji abinda take faɗa yabar wajen. Sai alokacin Yaya Abba ya lura da yayan itatuwan ta data zubar yace. “Ya haka Khausar mai yasa bakya kallon gabanki in kina tafiya?”. Cikin rawan murya tace. “Tsautsayine”. Tafaɗa tare da barin wajen aranta kuwa tunani take yau kuna Moddibo Arugar mu me ya kawo sa? kuma mai ya haɗa sa da yaya Abba? to me ya zoyi? da wannan tunanin ta isa Bishiyar ƙare zancenka tana isa ta hau kan dutse. dake farko ta zauna tare da sa hannunta ta riƙe reshen, kana ta kiran number Mommy. Shi kuwa Moddibo bayan sun karasa wajen Baffa Jauro. yace. “Ina yini Baffa fatan mun same ku lafiya ya kuma ƙarin haƙuri?”. Baffa Jauro kuwa cikin yanayin sauƙin kansa da kuma dattako ya amsa da. “Haƙuri Alhamdulillah fatan kunzo lafiya?”. Moddibo ya amsa da. “Lafiya Ubangij Allah yajiƙan sa da rahma idan kuma tamu tazo Allah yasa mu cika da Imani”. Baffa Jauro ya amsa da. “Ameen”. Yaya Abba ya kalli Baffa Jauro da faɗin. “Bari muje na rakasa Bishiyar ƙare zencen ka kuma Baba Yace kaje tare suke da Malam Arɗo". Kai Baffa Jauro ya gyaɗa kana yace. “Adawo lafiya”. Miƙewa sukayi suka nufi Bishiyar ƙare zancenka tun kafin su isa Moddibo ke jiyo suturatai da dariyar mutane Aransa yace to lafiya dai. Suna ƙarasawa yaga tsoffi,Matasa,maza,da mata kowa maƙale da waya akunnensa ahankali kunnuwansu ke jiyo masa kamar sautin Muryan Khausar da mamaki ya ɗaga kansa gefen yamma idanunsa suka sauƙa akanta saman dutse kana kanta na bisa reshen Bishiyar. Aransa yace to ashe ga inda ta samo ɗabi'ar hawa bishiya wato garin ne dole sai akan bishiya ake waya wannan shine gado. Ya juya tare da kallon yaya Abba yace. “Dole sai na hau kan Bishiya zanyi wayar?”. Girgiza kai Yaya Abba yayi yace. “A'a ko akan dutsen ma zaka samu network”. Jinjina kai Moddibo yayi yace. “To ku maida ƙa'ida mana mata su hau kan duwatsu maza su hau kan Bishiya idan ya kama dole ne sai an hau kan Bishiya ko kuma ku maida lokacin yin wayar mata daban lokacin yi. Wayar maza da ban kusa tsari da ƙa'idar musulunci ku dena gwamutsuwa haka”. Jinjina kai Yaya Abba yayi yace. “Gaskiya ne kabamu shawarar data dace Insha Allah za'ayi haka zan faɗawa Baffa Jauro ayi haka”. Moddibo kuwa cewa yayi. “Ai ya kamata ayi haka yanzu Meye amfanin ga mata asama sannan ga maza aƙasa ko kuma duk suna gwamutse maza da mata ko da duk kan ku 'yan uwane ai yakamata ayi abu duka bisa tsarin Addini ko ba haka ba bai dace ba duk da cewa yawancin ku ’yan uwane amma akwai auratayya atsakanin wasu”. Cikin jin daɗin Nasiyyar da ya masa da gamsuwa Yaya Abba yace. “Hakane Insha Allah za'a gyara malam”. Ita kuwa khausar sam batasan Moddibo sun zo wajen ba. Bayan sun gama gaisawa da Mommy. Mommy tace. “Khausar kwana biyu baki kira ba kuma kinsan ba zai yiwu na kira kiba”. Araunane Khausar da mutuwar Baffa Umaru ya dawo mata sabo tace. “Mommy ankashe Baffa Umaru har gida aka kashesa Mommy agaban idanuna aka kashesa!”. Shi kuwa Moddibo hankalinsa na kan yiwa Yaya Abba magana bai san mai take faɗa ba juyawar da zai yi yaji tana cewa. “Mommy har anyi sadakan bakwai hankalina ne bai kwanta ba”. ta faɗa hawaye na zuba daga idanunta. Shi kuwa Moddibo ido ya zuba mata ganin yanda hawaye ke kwaranya daga idanunta. Khausar tace. “Mommy ai zakizo kiyi mana ta'aziyya ko?”. Mommy da mutuwar ya kashe mata jiki tace. “Insha Allahu zamu zo, nasan idan na faɗawa Abbanki ba zai hana ba, ki shirya idan nazo zamu taho tare, dan Asma'u tazo tayi min magana batun zaku koma makaranta, kishirya kayanki idan muka zo zamu tafi tare idan Hajja Nana ta yarda”. lumshe Idanunta tayi tace. “Baza ma ta hana ba Insha Allah idan kunzo zamu tafi tare dan dama tace zanje Ɓadamaye wajen Baffa na nacan kuma sunzo ta'aziyya mun haɗu dasu, sannan ma Addata Ikki tazo mun haɗu da ita sai wani lokaci zanje Ɓadamaye nama karɓi number su, suma sunce dan suna sauri ne kuma mun haɗu amma da zasu je su duba ni anma munyi canjin number”. Cikin sanyi Mommy tace. “Toh shikenan babu damuwa ki shirya idan nazo zamu taho Insha Allah gobe zamu zo ta'aziyya”. Sallama Mommy ta mata. Juyawar da zatayi Idanunta suka sauƙa akan Moddibo daya tsareta da ido saida ta kusa faɗuwa saboda tsoron ganinsa. Da ido ya mata alamar ta saƙƙo kafin ƙiftawa da Bismillah kuwa ta diro ƙasa. Kallon Dije dake jiranta tayi tace. “Mu tafi” Yaya Abba ya miƙa mata kwandon kayan Marmarin ta data zubar yace. “Gashi kin zubar dasu na ɗebo miki”. Kamar wacce aka fisgo maganar daga bakinta tace. “Banaso ka bashi na bashi”. Sai da ta rufe bakinta asannan ta tuna mai ta faɗa hannu Dije ta fusga tace. “Mutafi". Shi kuwa Yaya Abba gyara riƙon kondon yayi. Shi kuwa Moddibo ɗaya daga cikin duwatsun wajen ya samu ya zauna tare da kiran wayar M Jameel. M Jameel na ɗagawa Yayi Sallama. Amsawa Moddibo yayi tare da faɗin. “Kada kaje kata nemana nasan zaka ne meni bana nan sannan ka kira wayata kaji akashe ina wani ƙauye ne da mukaje da Malam Arɗo amma Insha Allah zamu dawo kafin Azahar". M Jameel yace. “Toh meyasa baka gaya min ba tun ɗazu”. Cikin yanayin shaƙuwa yace. “Nima zuwan ba zata ne, kuma lokacin nasan kana bacci”. Cikin sauƙe numfashi M Jameel yace. “Toh badamuwa Allah ya dawo daku lafiya”. “Ameen”. Yace tare da katse kiran. Bayan ankira sallan Azahar sun idar kai tsaye wajen motarsu suka nufa Yaya Abba ne ya zo ya miƙa masa kwandon kayan Marmarin da Khausar tace abashi. Cikin yanayin nutsuwarsa da kuma sanyin murya sa yace. “A'a Nagode amma ka ajiye awajenka” Murmushi yaya Abba yayi yace. “To ai bani ce na baka ba Khausar ce tace abaka”. Yana gama faɗa ya buɗe bayan motar ya saka masa. Malam Liman ma ya basu Zabbi Baffa Jauro kuma ya aiko musu da ƙwan Zabbi Hajja Nana kuma ta aiko musu da zuma sannan suka yi musu sallama suka tafi Moddibo kuwa yaba karamci ci halaccin mutanen sukayi. Suna shiga cikin gari ya wuce da Malam Arɗo gidansa ya ajiye sa sannan ya sauke masa ƙwan Zabbin da kuma Zabbin da goran zuma. Malam Arɗo yace. “Ka ɗauki Zabbin da kuma ƙwoyin mana”. Kai Moddibo ya girgiza yace. “A'a wannan zumar ma ya isheni”. Ya ida maganar tare da jan motar ya fice zuwa gidansa. Acan ɓangaren Mommy kuwa da daren ta samu Lamiɗo ta faɗa masa maganar rasuwar da kuma son zuwanta suyi ta'aziyya, Cikin jimami yace toh Allah ya kaimu gobe zasu zo. *WOHOHO IN KAJI ANA ƘI GUDU TABBAS SA GUDU NE BEZO BA* _Ina kuke Ma'aurata masu sha'awar ganin sun zama taurari kuma fitilu a idanun mazajensu Uwar gida,Amarya,Tsakar gida,hadda tan kaɗen gida Shararriya kuma ƙasaitacciya data saba kawo muku nau'ikan sirrin sahihan magungunan ma'aurata wato *AYSHA ALIYU GARKUWA* Garkuwar Marubuta ayau ma ta dawo muku da Ingantattun magungunan mata masu kyau da inganci domin gyara kanki ki zamto tauraruwa a idanun mijinki...Muna da Ingantattun Abubuwa kamar haka_ :_Munada Garin mallaka, garin maɗi, garin Hakkin mayi, garin ɓelɗamhi Garin ilanwaddihi, Gumbar da ba'a baiwa mai kishiya, Gumbar kolli mai kellin al'khairi, Gumbar Riɗi wato 3 in 1, Gumbar makwaranyi, Masin Maliƙi mai masifar ƙarfi da matse mace, ka masin Daɗi har Maɗigan Akwai, kwanon ƙasaitacciyar mace mai masifar kyau da ratsa jiki da samar da inƙantacciyar ni'ima yanada abubuwa masu kyau haɗinsa, Zumar goron tula mai masifar kyau, tsumin dabino, mai ratsa jiki, tsumin Riɗi mai ƙarfi, Furar Mata mai tsastsafo da ni'imantaccen damshi, Cida kaza, Ciccibi Abodi, Tsumin Ɓaure, tuwon ɓauren, kana akwai maganin sanyi sadidan, da dai sauransu...Se kuma fannin ƙamshi kasance da Shu'umin ƙamshi wanda ze gigita ƙwaƙwalwar Oga tare da jin ko wacce mace bata kaiba...._ _Shin ko kina da labarin Miskilinci da ƙasaitar Rayyan Naaan amma lokaci ɗaya ya zamto zautacce sakali akan soyayyar Jannart bakomai Jannart ta riƙe ba face sirrinkan gyara da kuma shu'uman humran da kulaccar sirri na Aysha Aliyu Garkuwa(Tubali) tabbas taga tasirin haka domin Naanunta ya zame mata tamkar bawa_ _Shin ko kinsan sihirtaccen haɗin da Aysha ke sha kenan ta zamto tauraruwa a idanun Hamma Yusuf(Miwasmiti)...Tabbas Mahmud ya zamto zautacce kuma makaho akan sauyayyar Bazawara wato khadijarsa duk da kuwa gashi da budurwa(Namiji Baya Kaɗan) ko kinsan hakan nada alaƙa da amfani da sahihan maganin da kuma shu'uman humran Aysha Aliyu Garkuwa??.Nasan ba zaka ku manta da irin kima da kuma darajar da Aysha ke dashi acikin Idanun Sheik Jabeer ɗin ta duk da kuwa shekaru sunja anma jinta yake tamkar budurwa 'yar sha bakwai(Garkuwa) sirrin hakan na tare da Ingantattun kuma sahihan magungunan Aysha Aliyu Garkuwa Wato Garkuwar Marubuta da kuma Ma'aurata na tabbata kunsan da cewa basirarta ba'a iya rubutun littafi ya tsaya ba hadda inganta rayuwar ma'aurata ta hanyar kawo musu Nagartattun abubuwa Ga duk wacce ta shirya saya seta tuntuɓi number ta 09097853276 muna iya tura kayan mu aduk inda kuke afaɗin Nigeria harma da ƙetare Dan Allah 'yar uwa idan baki shirya siyaba kada kiyi min magana muɓatawa kanmu lokaci...._ 🤝🏻🤝🏻🤝🏻🤝🏻🥰😘sai.kunzo. sayan na gari maida kuɗi gida, Washe gari Da safe suka ɗauki hanya zuwa Rugar Jauro Yaya sukayi ta'aziyya. Bayan sun gama gaisawa ne Mommy tace. “Hajja Nana zamu koma da Khausar dan gobe Insha Allah zasu koma makaranta”. Kai Hajja Nana ta gyaɗa dan mutuwar ƙaninnata yasa tayi sanyi baki ɗaya. Tace. “Badamuwa ku koma da ita amma idan an kwana biyu ta riƙa zuwa saboda su saba da ‘Yan uwanta”. Kai Mommy ta gyaɗa kana tace. “Badamuwa Insha Allah zata zo”. Kasancewar dama Khausar ta haɗa kayanta tun daren jiya yasa ta dauko jakarta sai kuma ta Rungume Hajja Nana tace. “Hajja Nana zanyi kewarki ki riƙa zuwa bishiyar ƙare zancenka kina kirana dan Allah”. Murmushi Hajja Nana tayi kana tace. “Sai kace kin damu dani bayan rashin kunya kike min". ƙaramin bakinta ta tura tare da ficewa tana cewa nidai zanyi kewarki. Baki ɗaya Kakannints suka rakata jikin mota bayan sun haɗa mata tsaraba iri-iri Kama daga, Zabbi, Kaji, Ƙwan Zabbi, Nono jarka-jarka da kuma zuma man shanu. Kawai sai Khausar ta fashe da kuka cikin raunin murya. Tace. “Aranan da nazo kamar haka da Baffa Umaru aka tareni yau kuma gashi babu shi!". Hannunta Baffa Garga ya riƙe cikin rauni da zuba hawaye yace. “Kiyi haƙuri Khausar haka rayuwar take idan kaini yau gobe ba kai bane, kuma in sha Allah zasuga SAKAYYAH”. Hawayenta ta share tare da shiga mota tana ɗaga musu hannu Dije ma kan sosai tasha kukan rabuwa da Khausar. Fatan sauƙa lafiya suka musu sannan suka ja motar suka tafi. Khausar kuwa motarsu na isa harabar gidan Haiydar, Raudat da Ramadan suka taho da gudu suka rungumeta Ramadan ne yace. “Addah Khausi nayi missing ɗinki”. Kansa ta shafa tare da cewa. “Nima nayi missing naku”. “Addah Khausar Barka da dawowa daga zuwanki har gidan yayi haske, amma da bakinan duk saiyayi duhu”. Cewar Haiydar Ta wani wara manyan Idanunta tace. “Kada kayi masu gidan suji” ta faɗa tare da ɗaukar Ramadan suka shiga ciki afalon suka zube suna ta hiran bayan rabuwa. Cikin sakin fuska Khausar ta kalli Raudat dake zuzzuɓura baki tace. “A'a My happiness sis ya akayi ne?”. Baki Raudat ta kuma turawa tare da cewa. “Ba wani ai naga kinfi son Ramadan”. Dariya mai sauti tayi tare da jawota ta ruggumeta. Kana suka ci gaba da hirar yaushe gama. sallah kaɗai ke ɗagasu. Bayan kwana biyu ya kama yau Asabar zasu koma makaranta kasancewar Asabar ne farkon satinsu Alhamis da juma'a kuma Weekend. Tun wuri Khausar ta tashi bayan ta idar da sallar asbah tayi Azkharul sabah toilet ta shiga tayi wanka kana ta fito ta zauna gaban dressing mirrow ta shafe jikinta da lotion ɗinta kana ta shafa kajol a manyan Idanunta masu haske sai kuma ta shafa lips dinta Kaɗan tulin sumar kanta dake tsefe ta sanya farin Ribont ta kama ahankali ta buɗe duro ta ɗauki uniform ɗin ta dake goge maroon din wandon ta fara sanya wa sannan tasa ka farin riga sai kuma ta ɗauki farin ɗankwali ta ɗaura kana ta ɗauki maroon din hijab ta Sanya Wanda ya tsaya gwiwarta wani irin kyau tayi na ban mamaki sosai Uniform din ya amshets tamkar dan ita akayi. A gaban Dressing mirrow ta tsaya ta ɗauki kwalban turare sun kai kala biyar ta feshe ilahirin jikinta dashi sannan ta ɗauki combos Fari ta Sanya tare da ɗaukar school bag ɗinta ta rataya kana ta fito falo. Murmushi Mommy tayi tace. “Manana kinyi kyau”. Ta juya manyan Idanunta tace. “Nogode Mommy na”. Haiydar kam murmushi yayi yace. “Yau za'ayi ruwa da ƙanƙara shugaban ’yan letti ta riga kowa shiryawa”. Harara ta maka masa batare da tace komai ba ta shirya Raudat sannan sukayi Breakfast suka shiga mota Amina sai Harara take watsa mata ita kuwa khausar bata ma san tana yiba domin aƙasan ranta tunanin haɗuwarta da Moddibo take da kuma irin hukuncin da zai yanke mata. Suna isa Makarantar lokacin har anfara shiga class cikin sauri sauri Khausar ta riƙe hannun Raudat suka nufi side dinsu Raudat ta ajiyeta a class kana da sauri ta juya, zata fita class ɗin kenan. Taji Raudat ta saki ƙara tare da kiranta. Da sauri ta juya tare da kamo Raudat ɗin da taga tana jujjuyawa, tsugunawa tayi tare da cewa. “Raudat menene ya faru”. Cikin kuka da yarfa hannu Raudat tace. “Wayyo idona Adda Khausy ido, borkono". Da sauri ta jawota tare da fara hura mata idon. Sai kuma ta amshi goron ruwar da Antin su ke miƙa mata. Wonke mata fuskar ta ta farayi tare da murza mata idon. Cikin Sa'a kuwa ɗan abin da ta shiga idon ya fita. A hankali ta buɗe idann nata, da tuni yayi jazir. Cikin sanyi tace. “Ayyah Raudy na sannu ko, yanzu dai ya fita ko?”. Kai ta gyaɗa mata tare da kama hannun Antin nasu. Ganin hakane yasa Khausar juyawa da sauri ta fito ta nufi harabar makarantar. Shiru ba kowa a tsakiyar harabar alamun an gama shiga class kenan. Cikin sassarfa ta fito daga side din ’yan nursery. Kana ta nufi sude ɗinsu. Da sassarfa ta nufi kan step ɗin. Dai-dai lokacin kuma Moddibo ya fito daga class dinsu ya nufi ƙasa, a hankali yake take steps din yayinda hankalinsa baki ɗaya yana kan....! Ki biya ki karanta, kiji ainin manufar labarin kiyi dariya kiyi shauƙi kibi haushi kiki tausayi kiyi kuka. Kiyi murmushi By *GARKUWAR MARUBUTA* [19/07, 7:44 PM] Halimatu A/rahman Sadeeya: 📝🍇✨💫⏰🤴🏻👹❤️❤️❤️🍇 *SAKAYYAH* _Page 9_ NA *AYSHA ALIYU GARKUWA* 🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 *FREE PAGE NE ƴar uwa ki biya ki karanta abinki cikin Salamah, littafin SAKAYYAH 1k ne kacal 0661110170 GTBank AISHA ALIYU GARKUWA sai ki turo min shaidar biyanki ta WHATSAPP 09097853276. Kana in saki a Groups da na buɗe ba SAKAYYAH in da zaki karanta abinki salamun ƙaulum min rabbil rahim. Nama lfy fata lfy. Ba ruwan ki da jiran na sata na Allah ya isa* Cikin nitsuwa yake tafiya, tare da taka steps ɗin a hankali, yana sauƙa ƙasa, yayinda hankalishi baki ɗaya ke bisa system nashi dayake kan hannunsa na dama yana daddanashi da hannun hagunsa, bisa dukkan alamu. Abu mai mahimmanci ne yakeyi. A dai-dai lokacin kuma Khausar ta iso bakin steps ɗin, cikin sauri take tafiya, da alamun tsoron kada malami ya rigata shiga aji ne. Da sauri take tattaka steps ɗin tanayi sama. Steps biyu ta taka ana uku, taji juyo da kanta da sauri dan jiyo muryar M Jameel na ce mata. “Khausar sai yanzu?”. Ba tare da ta tsaya ba, kana bata kuma juyo kanta ba taci gaba da tafiya a haka, hannunta na kan da ƙarfe dake gefen steps ɗin cikin yanayin sakewarta da M Jameel ɗin tace. “Wallahi tun ɗazu muka iso fa Malam”. Yana mai binta da ido yace. “To kuma meya hanaki shiga class?”. Still bata janye kanta daga kallonsa ba, kana bata tsaya daga haurawa saman da takeyi ba tace. “Raudat ce ta tsaidani a side ɗin su”. Da sauri yace. “Da me ta tsaida ki?”. Ɗan guntun murmushi tayi tare da cewa. “Wai ƙwarone ya shiga idonta, shinefa tai ta ihu taƙi sakina dole saida aka cire matashi Allah sai kaga yadda idonta yayi jazir”. Kanshi ya sunkuyar yana ɗan murza zaɓen azurfan dake yatsar yace. “Ayya kwaro bai kyauta ba ya shiga idon Gimbiya Raudat”. “Ai dai kam fa”. Ta faɗina tana mai ƙoƙarin juyo kanta. Cikin tsokana yace. “Gashi kuwa har Malam Moddibo ya shiga ajinku”. Cikin sauri ta kuma juyo kanta da dama bata gama juyashi ba cike da kaɗuwa tace. “Da gaske?”. Kai ya gyaɗa mata tare da cewa. “Tun ɗazuma kuwa” Cikin yanayin tsoro ta ɗan zaro manyan udanunta tare da cewa. “Na shiga ukuna”. Murmushi M Jameel yayi tare da cewa. “Ato kiyi sauri ki hau, in kinyi sa'a ya barki ki shiga”. Jin haka yasa ta juyo da sauri tare da taka step ɗin gaba kana tayi kwanan haurawa kam steps ɗin da zai sadata da sama. Wanda kuma dai-dai lokacin Moddibo ma ya taka step na ƙarshen kwanan. Unexpected taji tayi karo da mutu. Shi ma Moddibo ba zato ba tsammani yaji kanta ya bugi ƙirjinsa yayinda hannunta ya bugi System ɗin dake hannunsa ya subce ya tafi ƙasa da sauri ya sunkuyo ya cafe system ɗin da kana ya miƙe tsaye, Ita kuwa Khausar cikin sauri ta ɗago kanta dai dai lokacin kuwa ya ɗago kansa shima ido cikon ido suka kalli juna kamar a fuzge ya furta. “Again?”. a lokacin guda kuma, cikin tsananin takaici da zafin rai ya ɗaga tafin hannunsa na hagu ya yarfa mata wani irin gigitaccen mari mai masifar zafi gami da raɗaɗi. M Jameel kuwa jin sautin sauƙan marin ne yashi ɗago kansa da sauri. Ita kuwa Khausar wani irin gigitaccen ihu mai cike da rauni tare raɗaɗi ta saki, tare da dafe kuncinta kana ta rumtse idonta wanda duhu mai tarin yawa ya mamaye mata gani, kana tayi taga-taga ta koma baya zata faɗi, jin ta tafi suuuuu ƙafarta ta sule yasa takuma sakin wani ƙaran tare da buɗe idanunta, sai kuma tayi sauri ta medasu ta rufe sabida ganin wasu irin taurarin masu wutsiya da tartsatsi suna gilmawa ganinta sabida zafin marin da yasa suka mamayewa ganinta. Gaba ɗaya ta sadakar domin tasan muddin ta faɗo nan to ita da karaya sun zama aminan juna. M Jameel kuwa kanshi ya riƙe da hannu bibbiyu tare da faɗin. “Innalillahi!!”. Wanda faɗin hakane ya jawo hankalin Malam isa da yazo wucewa ta gefensa. Shima ma Malam isa idonsa ya rumtse da ƙarfi tare da cewa. “Yah Salam”. Shi kuwa Moddibo cikin takaici yayi sauri miƙa hannunsa da nufin kamo hannunta amman ina tuni tayi nisa. Sai yatsunta biyu ya samu ya riƙe da masifan ƙarfi. Wanda saida suka bada sautin ƙas-ƙas. Cikin zafin nama ya fincikota da ƙarfi wanda hakan yasa ta afka jikinsa. Ita kuwa Khausar jinta a jikin mutum ne yasa tayi masa wani irin sahihin rugguma mai cike da razani dan gani take kamar dai har yanzu bata tsira ba. Kanta ta cusa cikin ƙirjinsa tana mai shaƙan turarensa mai masifar ƙamshi. Wanda a take nitsuwarta ta fara dawowa. Shi kuwa Moddibo cikin tsoro da wani irin masifeffen abu da yaji ya soƙi tsakiyar kansa har zuwa cikin ƙahon zuciyarsa kana ya harba masa wasu irin masifaffun baƙin al'amuran a cikin jijiyoyin jikinsa da suka sa jikinsa sakin wani irin masifeffen karkarwa da sabauta aniyarsa, ya ware hannunsa tare da rumtse idanunsa da masifan ƙarfi. M Jameel kuwa ajiyan zuciya mai ƙarfi ya sake tare da jingina bayansa da jikin ƙarfen. a hankali ya kuma sakin numfashi tare da kallon yadda Moddibo ya buɗa hannayensa duka biyu kana ita kuma Khausar tana kwance bisa ƙirjinsa tayi lip tana ruggume dashi da masifan ƙarfi. Wani irin shu'umin dariya mai sauti M Jameel ya sake. Wanda hakan yasa Moddibo buɗe idanunsa kana dai-dai lokacin yaji gaba ɗaya tsikar jikinsa na tashi. Malam isa kuwa sunkuyar da kansa yayi yana murmushi. M Jameel kuwa dariya yake tare da nuna Modibbo da Khausar ɗin wacce tuni fuskarta tayi jazir shatin yatsun hannunsa sunyi ruɗu-ruɗu a farar fatarta. Cikin sauri Moddibo ya ɓalle hannunta daga jikinsa tare da matsawa gefe da sauri. Wani irin tsuke fuskarsa yayi tare da watsa mata kallon da yasa hantar cikinta kaɗawa. Wanda cikin rawan jiki da rawan murya cike da rauni tace. “Ana Aspet ya Mu'allim Allah mi larai ma on! Please! Kayi haƙuri”. Ta ƙare mgnar cikin tsoro tare da gwamusa yaruka hudu duk a wuri ɗaya dan neman afuwa. Shi kuwa Moddibo juyawa yayi tare da ratsa gefenta ya wuce kana cikin wata fusatacciyar murya mai matuƙar firgitarwa yace. “Biyoni!”. Cikin ɓarin jiki tace. “Toh”. Sannan ta miƙe tabi bayansa. M Jameel dake riƙe da System ɗin yana juyawa yayi saurin bin bayansa da faɗin. “Alhamdulillah kamar babu abinda ya samu System ɗin”. Shi dai Moddibo ko juyawa baiyi ba bare kuma ya tankawa M Jameel. Malam Isa kuwa dake ƙasa ido ya zirawa Khausar dake sauƙwa dafe kuncinta da kunne ya da tun da tasha marin ya bada sautin kauwww har yanzu ƙaran takeji, kana ga idanunta da suka kaɗa sukayi jawur asanda ta saƙƙo yace. Fattanah sam bakya yin abinda ya dace a rayuwarki”. Cikin zafin raɗaɗin marin da fuskarta keyi ta ɗago Idanunta da suke sake girma da ja ta kalli Malam Isa sai kuma tace. “Wallahi bansa niba ne na juya ina kallon Malam Jameel ne dake yimin magana ne mukayi karo”. Bata jira jin abinda zai ce ba tabi bayan M Jameel dake biye da Moddibo. Cak Khausar ta tsaya daga bakin Office ɗin, karo na farko kenan arayuwarta da zata fara shiga Office ɗinsa, duk da cewa da basu da office da yawa, amma yanzu gyaran da akayi an haɗa Malamai biyu akan Office ɗaya Office din ba wasu masu girma bane, haka zalika ba ƙanana bane, sannan duk kusan ajere suke. Ahankali Khausar ta maida Idanunta bakin office ɗin da akasa wasu irin flowes masu launi mai kyau da ɗaukar hankali aka jera suna fitar da wani irin sanyayyan ƙamshi. Cikin Office ɗin kuwa Madaidaitan deks ne da kujeru ɗaya na fuskantar gabar ɗaya na fuskantar yamma daga gaban ko wanne kuma akwai kujeru guda biyu daga kan deks ɗin daga gefen damar sa akwai wani Cubet kamar kanta dake ɗauke da tarin littattafai na addini da kuma na boko cikin wajen kamar dai Library haka wurin yake. Daga gefen hagunsa kuma flowes ne masu kyau da tsari daga jikin bangon kuma Room hitane ne maƙale abango yana fitar da ɗumi mai daɗi a jiki, Sai kuma labulayen window da suka kasance farare sol Sanyayyan iska na kaɗawa daga bangon kudu dake kallon yamma TV ne maƙale abango daga tsakiya kuwa wani irin dakekken turkey carpet mai yawan gashi fari sai ratsin maroon kaɗan. sosai Office ɗin yayi kyau. Shi kuwa Moddibo cikin nutsuwa da kuma zafin da zuciyarsa keyi masa ya zauna akan kujeran dake gabar yana fuskantar yamma yayin da M Jameel ya zauna akan kujeran dake yamma yana fuskantar gabar kana da sunan ko wannensu ajiki kujerarsa. Ita kuwa khausar cikin tsananin tsoro ta ƙarasa shiga office ɗin tare da tsugunnawa agaban table ɗin da Moddibo ke zaune. Ta riƙe kunnenta Muryanta Araunane wanda ke nuni da tsantsar tsoro da tashin hankali tace. “Malam kayi haƙuri bansan kana tahowa ba”. Shi kuwa Moddibo ko kallonta baiyi ba saboda yanda zuciyarsa ke tsananin ta farfasa ya tabbata idan yace zai daketa to zai iya karyata ko kuma ya sumar da ita hakan yasa ya janyo kujeran dake kusa dashi ya ɗaura ƙafafunsa akai kana ya lumshe idanunsa tare dasa hannu ya janyo Hiramin dake kansa ya rufe saman Idanunsa. Cikin tsantsar nutsuwa da kuma sanyayyan sautin muryarsa mai zaƙi ya fara rara Ƙira'a acikin suratul Rahman yasan hakan shine kaɗai zai sanyaya masa ransa da zuciyarsa yasan muddin yace zai daketa ayanzu zai iya sumar da ita ko kuma karyata. Saboda abubuwan da yarinyar ke masa yayi yawa. Sabida tsabar raini da rashin kunya fa har gidansu ta bisa tayi masa rashin kunya sannan ta jima sa ciwo ayatsun ƙafansa wanda ya ɗauki tsawon kwanaki yana fama da ciwo. Kana yaje ƙauyen su nan ma bata barshi ba saida ta bisa tayi masa rashin kunya ta nemi jefa shi acikin ruwa da wannan masifeffen sanyin garin nasu, kana amakaranta ma bata barsa ba shin tsaranta ta mayar dashi kome?. Ita kuwa khausar cikin Sanyayyar Muryanta me cike da tsoro tace. “Ayyah malam na tuba kayi haƙuri wallahi bansani bane”. Ƙin tanka mata Moddibo yayi ya cigaba da rera karatunsa cikin zazzaƙan muryansa. Shi kuwa M Jameel Gyaran murya yayi hakan yasa Khausar tayi saurin Kallonsa da manyan Idanunta da suka kaɗa sukayi jawur. Da ido yanuna mata Moddibo alamar ta cigaba da basa haƙuri. Kai ta gyaɗa sannan ta cigaba da cewa. “Ayyah Malam na roƙeka kayi haƙuri bazan sake ba”. Acan sama ajinsu Khausar kuwa wani irin tsarin gini ne mai matuƙar kyau da ɗaukar hankali wasu irin windon Glass ne tsala-tsala masu tsayi da kyan tsari sannan ga flowes masu fitar da sanyayyan ƙamshi kana ga Room hita guda biyu gaba da baya daga farkon shiga class ɗin kuwa wani irin Black Board ne mai tsari irin wanda ake amfani dasu a manyan makarantu, kana ga wasu irin kujeru na zaman ɗalibai masu taushi da kyau, agaban ko wani kujeran ɗalibi akwai sunan sa ajiki, hakan yasa duk ɗalibar data shiga baza tasha wahala neman wajen zamanta ba wanda kuma manna sunan ake bisa alamu in an tashi kawai ɓarewa za'ayi a saka sunayen sabbin waɗanda zasu shigo ajin, kujeran Khausar shine na farko acikin jerin kujerun dake gaba da sunanta manne kamar haka _Khausar Usman Abubukar Lelewal._ Samira Sani ce ta ɗan juya Idanunta kan kujerar dake gefenta. Wanda sunan Khausar dake manne kujerar afarkon. Wani irin ya mutsa fuska tayi tamkar wacce taga wani abin ƙi cikin taɓe baki da tsanar mamallakiyar sunan tace. “Ikon Allah wannan shine suna mai buƙatar hadda sunaye huɗu duk masu tsawo!”. Ta Ida maganar tare da bankawa kujeran harara tamkar Khausar ɗin na kai, kana ta zauna daga baya inda sunan ta ke kai. Asma'u dake gefe azaune tace. “Ha'a sunane de ai ba wani abu ba kuma duk sunayene masu inganci da Kekkyawar nasaba naga dai sunanta sunane na ɗiya ga Annabi Muhammad (S.A.W) sannan sunan mahaifinta sune na sahabin Manzon Allah (S.A.W) haka zalika sunan kakanta sune na sahabin Manzon Allah (S.A.W). Lelewal kuwa naga suna ne da kowa ke fatansa”. Abeeda Sule ne ta watsa wa Asma'u harara tare da faɗin. “Ke kuma wayasa bakin ki?”. Taɓe baki Asma'u tayi kana tace. “Ai gaskiyane daga kallon sunan baiwar Allah zata fara ƙanan magana”. Ɗaya daga cikinsu manyan matan ajin nasu ne wacce bata fiye magana Hajia Khadija tace. “Da wannan hatsaniyar da kukeyi tunda Moddibo ya fita tun ɗazu akan zaije ya dawo bai dawo ba aigwara kuje ku duba ko lafiya mai ya tsaida shi aji ba kowa kuma shine muke da First period?”. Cikin zumuɗi Samira Sani tace. “Gaskiya ne kam bari naje na kirasa”. ta ida maganar tare da ficewa ta sauƙa ƙasa. Cikin yauƙi ta nufi Office Tana isa idanunta suka sauƙa akan Khausar dake riƙe da kunnenta, ga kuma Idanunta da suka sauya, yayin da shi kuwa Moddibo idanunsa ke lumshe yana rera karatun Alkur'ani cikin Sanyayyar sautin muryansa daya haɗu da ɗumin room hita ga ƙamshin daddaɗan tularensa. Numfashi mai nauyi ta fesar tare da tsirawa yalwataccen sajensa daya ƙawata kyawun fuskarsa idanu sai kuma ta maida kallonta kan zara-zaran yatsun hannunsa dake kan table yana ɗan bubbugasu ahankali cike da shauƙi tace. “Wowww”.Faɗar hakan da tayi shi ya janyo hankalin M Jameel yayi saurin juyawa ganinta tsaye acikin Office din yasa shi faɗin. “Lafiya?”. Sai asannan ta dawo cikin nutsuwarta still Idanunta na kan Moddibo tace. “Malam Barka da safiya”. “Barka dai”. Still idanunta na akan Moddibo tace. “Malam dama munzo kiran Malam Moddibo ne, shine muke dashi tun ɗazu ya sauƙa, akan cewa zai zo ya ɗauki wani abu sannan kuma bai koma ba”. Da ido M Jameel ya nuna mata Moddibo da har zuwa lokacin idanunsa ke lumshe yana karatu sai dai ya rage sautin muryansa ya koma fita asaman laɓɓansa. Shi kuwa Moddibo jin Muryanta yasa ya janye Hiramin dake fuskarsa kana ya buɗe idanunsa da har zuwa yanzu akwai alamun ɓacin rai acikinsu, kallo ɗaya ya mata ya kawar da kansa gefe. Ita kuwa Samira gefe ta koma ta tsaya. Khausar kuwa lumshe Idanunta da suka kaɗa sukayi jawur tayi sai kuma ta buɗe su still Hannunta nakan kunnenta tace. “Ayyah Malam kayi haƙuri”. Shi kuwa Moddibo juyawa yayi tare da kallon M Jameel yace. “J ka da keta”. Da sauri M Jameel ya juya tare da nuna kansa da babban yatsa kana yace. “Ni!?”. Cike da tsuke fuska Moddibo ya gyaɗa masa kai kana yace. “Eh ka daketa!”. Zare Ido M Jameel yayi tare da cewa “Meyesa?”. A kufule Moddibo yace. “J kadaketa nace!”. Kallon mamaki M Jameel yake masa tare da cewa. “Akan me zan daketa?”. Cike da ɓacin rai Moddibo yace. “Idan fa ka bari nace ni zan daketa zan sumar da ita fa!, zan karyata fa!!”. Cikin tsananin fusata ya ida maganar. Ita kuwa Khausar tuni jikinta ya hau rawa Allah ya sani bata son duka, sannan mari ɗaya daya mata ya mugun gigita mata ƙwaƙwalwa wanda har zuwa yanzu take jin raɗaɗin sa asaman fuskarta. Fuskarsa babu walwala yace. “Idan har nace zan daketa zan sumar da ita”. Ita kuwa Khausar jin azaban mari ɗaya daya mata, aranta tace Ashe Allah ya rufa min asiri da yasa duk lokacin da nayiwa Moddibo laifi baya duka na yake sa Malam Adam display master ke dukana na tabbata dashi yake dukana kullum da tuni ya kasheni!. Cikin hanzari ta juya tare da kallon M Jameel ta miƙa masa hannu Muryanta na rawa tace. “Malam ka dakeni!”. Girgiza kai M Jameel yayi cikin sanyin murya yace. “Ni dai kam bazan iya ba bazan iya dukanta ba Moddibo, ka dubi fuskarta fa mari ɗaya da ka mata kalli fuskarta fa ai ya wadatar wani hukunci ya rage bayan wannan?”. Ya kare mgnar a hankali Moddibo kuwa cikin fushi yace. “Kada keta in kuma baza ka daketa ba zan daketa da kaina fa”. Cikin sauri M Jameel ya fara girgiza kai yayi cikin wata Sanyayyar murya me cike da zallar jin ƙai tare da tarin tausayi gami da rauni yace. “La! La!! La!!! A.J bazan iya ba! Wlh Bazan iyaba ba wannan ba hurumina bane hurumin taɓa ta awajenka yake bani da karsashi ko ƙwarin gwiwar da zan iya taɓa ta!”. Ya ida maganar cikin wani irin salo na daban, kana dai-dai lokacin Amina tazo Office ɗin domin kiran M Jameel ya shiga ajinsu wani irin sarawa kanta yayi jin yanda yake cewa bazai iya ba. Da sauri ta dafe ƙofar office ɗin jin jiri na ɗibarta kadde ace dokon soyayyarsa za tayi abanza, kadde Khausar yake so yanda ya ƙarashe maganar na nuni tamkar itace rayuwar sa. Da sauri Moddibo ya juya ya kalli M Jameel jin yanda yayi magana da kuma yanda ya lanƙwasa harshensa abun ya bashi mamaki. Azuciye Moddibo yace. “In daketa kenan?”. Langwaɓar da kai M Jameel yayi cikin sanyin murya yace. “Kayi haƙuri ina mai bada haƙuri amada dinta ka nemi wani punishment ɗin ka bata amadadin wannan, amma nikam bazan iya dukan taba sannan kaima banaso ka daketa!”. Baki ɗayan su kallon Mamaki suka bi M Jameel dashi ganin yanda yake lanƙwasar da murya tare da nemawa Khausar ya fiya, ita kuwa Amina wasu hawaye ne masu zafin gaske ne na tsananin kishi da baƙin ciki, suka zubo mata saurin ta sanya hannu ta share. Kwantar da Murya M Jameel ya kuma sakeyi ya cigaba da cewa. “Kallifa A.J mari ɗayan nan da kamata kalli fuskarta fa ka daketa awaje mafi daraja”. Moddibo kuwa lumshe idanunsa yayi kana ya buɗesu akan M Jameel tare da cewa. “J kadaketa ni idan nace zan daketa bazai mata daɗi bafa”. Sake Langwaɓar da kai M Jameel yayi kana yace. “Kayi haƙuri Moddibo ni bazan iya dukanta ba!”. Ita kuwa Samari Sani na tsaye agefe ta harɗe hannayenta aƙirji yayin da ta zubawa Moddibo ƙananun Idanunta ko ƙyaftawa ba tayi. Ita kuwa Amina Idanun ta nakan M Jameel da idanunsa ke kan Khausar zuciyarta nayi mata zafi. Khausar kuwa kallon M Jameel ta sakeyi akaro na barkatai tace. “Malam Jameel ni dai ka dakeni”. Kai ya girgiza mata tare da faɗin. “Bazan iya dukan ki ba Khausar!”. Shi kuwa Moddibo cikin tsananin ɓacin rai ya juya ya kalleta a kufule yace. “Toh inda keta da kaina!?”. Girgiza kai M Jameel yayi sai kuma yace. “A'a asassauta mana dan Allah”. Ƙwafa Moddibo yayi da faɗin. “Shikenan kije ki kaɗe ɗan kwali sau ashirin”. Cike da tsoro ta zaro ido domin kaɗe ɗan kwallon da yace yana nufin ta cire ɗan kwalinta tasa abokitin ruwa ta matse kana ta kaɗe har sai ya bushe, sannan ta sake sakawa cikin ruwa ta matse kana tayi ta kadewa har sai ya bushe. Tofa jin haka ne yasa a tsorace ta zare Ido Jin hukuncin daya yanke mata ba zata manta lokacin daya sata kaɗewa sau goma ba awannan lokacin ma saida tayi sati biyu gaɓɓanta na ciwo ko abu zata ɗauka da ƙyar take iyawa. Cikin yanayin neman alfarma M Jameel ya sake langwaɓar da kai kana yace. “Dan Allah ka sassauta mata karage mata”. Jin Muryan M Jameel yasa ita ma ta kalli Moddibo cikin wata raunatacciyar murya tace. “Dan girman Allah Malam kayi haƙuri karage min”. Shi kuwa Moddibo wani kallo ya watsa mata cikin haɗe girar sama dana ƙasa yace. “Kada ki sake haɗa ni da girman Allah da kinsan darajar girman Allah da zaki mutunta Malama ki, kije kiyi shabiyar kinci darajar girman Allah. idan kika sake cemin dan Allah in rage miki kuwa nida ke bibbiyu!”. Gyaɗa kai tayi kana tace. “Toh shikenan”. Shi kuwa M Jameel kallon Moddibo yayi cikin jujjuya ido yace. “Ina neman alfarma abarta tashiga aji tayi karatu idan antashi Break sai tayi”. Shi kuwa Moddibo Ɓata fuska yayi yace. “Bana son ganinta a aji Idan naganta a aji zan kakkaryata in wurgar ta window”. Ita kuwa Samira Sani cikin lanƙawasa harshe tace. “Malam Moddibo mu tafi”. Sake tamke fuska yayi tare da juyawa ya watsa mata wani bayyane harara sai kuma ya nuna mata ƙofa alamar ta ɓace masa da gani. Sum sum ta juya da sauri ta fice. Da harara yabi bayanta Aransa yace. Shegiyar yarinya mai kama da Mayya, sai shegen kallon jaraba tasani gaba zakiyi dan rashin kunya. Samira Sani kuwa tana shiga ajinsu ta lumshe Idanunta tare da kallon gefen ko wannen kujera dake ɗauke da flowes ta saki murmushi mai cike da jin daɗi, tasan wannan aikin Moddibo ne domin kaf cikin Malaman shike son flowers. Hajia Ruƙayya ce ta dubi Samira data shigo kana tace. “Ni kam ya banga Khausar ta shigo ba har yanzu kuma ɗazu na hangota kafin na haura”. Juye Ido Samira tayi tare da faɗin. “Tana can tayiwa Moddibo rashin kunya yana cin Ubanta, shegiyar yarinya fitsararriya ‘yar marasa tarbiyya!". Asma'u ce ta juya ta kalleta rai a haɗe tace. “Haba Samira meyesa zaki zagi iyayenta ai bai kamata ki zagi iyayenta komai yaya iyaye nada daraja”. Harara Samira ta wurga was Asma'u kana ta buɗe baki da niyyar magana ta fasa sakamakon shigowar Moddibo. Ganin shigowar Moddibo yasa ta tsuke bakinta tare da neman waje ta zauna cike. Cike da ladabi suka gaishesa cikin harshen larabci tare da faɗin. ”صبحل خير ىاعثتذ“ Ya Amsa da. “صبحل نور كىفل قراء“. Suka amsa da. ”الحمد الله“ Kasancewar Tafseer zasuyi dake yanzu lokacin Islamiyya ne yasa yace. “Kuyi muraja”. Cikin bawa ko wanne harafi hukuncinsa suka shiga karanta suratul Muhammad har zuwa karshe. Bayan sun gama kawo haddan ya jinjina kai tare da faɗin. “Sai gobe Insha Allah zamu fara tafsirin sa”. Aɓangaren M Jameel kuwa tare suka jera da Amina suka nufi ajinsu yayin da azuciyar Amina yayi baƙiƙƙirin data tuna yanda M Jameel ke karyar da murya akan Khausar har suka isa ajin tunanin da take aranta kenan yanayin yanda tsarin ajinsu Khausar yake haka ko wanne aji yake cike da ƙwarewa M Jameel ya shiga yi musu ƙarin Mi'atu Hadith daga na Arba'in bayan sun karanta masa. Ko wanne aji da Malami aciki suna darasi. Ita kuwa Khausar ita kaɗai ce tsaye aharabar Makarantar cikin gajiyawa ta ɗaga boket ɗin ruwan ta koma rana wai ko zata samu yafi bushewa da wuri, tsoma ɗan kwalin tayi aciki kana ta matse sannan ta fara kaɗewa. Nannauyan ajiyar zuciya ta saki tun akaɗewa na uku taji hannunta ya sage aranta tace. “Insha Allah Ina komawa gida zan nemi ɗankwali mai shara-shara mara nauyi wanda kodan irin rana ta yau ta faru zaimin sauƙi. Cike da gajiya ta miƙe ta riƙe ƙugunta da hannu ɗaya ta lumshe idanunta sosai ta gaji. Shi kuwa Moddibo daga can sama acikin ajinsu Khausar yake kallonta tana kaɗe-kaɗen ganin ta tsaye ta riƙe ƙugu gaban ƙirjinta duk ya jiƙe da fuskanta, ganin ta tsayanne yasa ya buɗe glass ɗin window dake saitin ta tare da ziro hannunsa ya ƙyasta yatsunsa da ƙarfi wanda hakab yaja hankalin Khausar da saurin ta ɗaga kanta. Ganin abinda yayi yasa da sauri ta cigaba da kaɗewa tana mai rintse Idanunta. Har Moddibo ya gama teaching ɗinsa ya fita Khausar nakan punishment Koda ya saƙƙo ya ganta Harara ya watsa mata kana a kufule yace. “Ba zaki shiga ajiba yau har sai kin gama abinda nasaki”. Fuska ta Shagwaɓe tare da langwaɓar da kai tace. “Ayyah Malam dan Allah kayafemin duk ɗan Adam ajizine!”. Harara ya watsa mata ya wuce batare daya bata amsa ba, bayansa tabi da kallo tana tura ƙaramin bakinta, to har wani malami ya sake shiga yayi darasi Khausar bata gama ba sai sha biyu dai-dai lokacin tashin matan Aure sannan Yara da ‘Yan mata suyi suci abinci su koma ajin boko. Hajiya Ruƙayya ce da Aunty Khadija ne suka fito tare da ƙarasawa kusa da Khausar dai-dai lokacin da Khausar ke faɗin. “Wayyo hannuna”. Ta faɗa tana matsa yatsunta dake raɗaɗi. Dafata Hajiya Ruƙayya tayi kana tace. “Ayyah sannu Khausar kece bakyaji me kika yiwa Moddibo!?”. Langwaɓar da kai Khausar tayi tare da marairaice murya tace. “Allah babu abinda na masa kawai ina tahowa ne mukayi karo dashi har System ɗinsa ya faɗi kuma ma naji malam Jameel yace System ɗin beyi komai ba amma sai da ya sani wannan kaɗe-kaɗen sabida in baici zalina ba baya jin daɗi rayuwarsa ta duniya”. Ta ida maganar da faɗin. “Affan zo”,tare da miƙa masa hannu. Murmushi Aunty Khadija tana mai jujjuya kai. Ita kuwa Hajia Rukayya Miƙa mata yaron dake ta faman ƙyalƙyala mata Dariya Aunty Ruƙayya tayi Sai kuma tayi saurin janye hannunta tana cewa. “Wayyo Aunty Ruƙayya hannu na ya gaji yaukam bazan iya riƙe sa ba”. Ta ƙare mgnar tana ƙara matsowa kusa da Aunty Ruƙayya kan kumatunsa ta sumbata tana faɗin. “Affan gaye". Shi kuwa yaron sai dariya yake ƙyalƙyala mata tare da miƙa mata hannu alamar yana so ta ɗauke sa dan sosai yaron ya saba da ita saboda Aunty Ruƙayya na zumunci da Mommy Khausar sannan Khausar na shiga lokaci zuwa lokaci. Samira Sani da Abeeda Sule ne suka ƙaraso wajen Kallon Abeeda Sule Samira tayi da faɗin. “Ai Moddibo shike maganin tantirai marasa mutunci ’ya'yan Fitsararru awannan makarantar yana min dai-dai!”. Sake hannun Affan Khausar tayi ta juya ta kalli Samira da kyau tace. “Waye ‘Yar marasa mutuncin? Akwai ‘Yar marasa mutunci daya wucike ne ‘Yar magulmata Munafuka kawai! Inbanda munafurci da gulma da biye-biyen bokaye Me kuka iya!?”. Afusace tace. “Ke Khausar zanci Ubanki fa!". Wara ido Khausar tayi kana tace. “Ubana kuma, uhmm saide Kici naki uban domin ni kam nawa Ubana tuni Ubangiji ya daɗe da yimasa sutura sai dai kije kici naki ‘Yar matsiyata?”. Ta ida mgnar cikin tsiwa,. Abeeda Sule ne tace. “Ke akwai ma ƴar matsiyata irinki, kina tsammanin bamu san cewa munsan ke Agwola bace acikin gidan sarki da kike nunawa kamar gidan ku ne?”. Dariya Khausar tayi kana tace. “Dan Allah rufe mana baki ‘Yar Alhaji sule baka layya kibari tukunna in Babanki ya fara layya saiki faɗa wa mutane Magana?”. Zare ido Abeeda tayi tare da hayayya ƙowa tace. “ ‘Yar iska ni zaki cewa Ubana baya layya”. Taɓe baki Khausar tayi tare da faɗin. “Ke rufe min baki ai bani na faɗa ba Inkiyarsa ce hakan, ko ba sunan sa bane? Alhaji Sule baka layya!! ko kuma ni nasa masa ko kuma dan tsoronki sai inki kiransa da sunan da aka sa mishi”. Hajiya Ruƙayya ce tace. “Khausar rabu dasu”. Gyaɗa kai tayi. Ita kuwa Samira cikin takaici tace. “ ‘Yar banza kawai agola”. Dariyar rainin hankalin Khausar tayi sannan tace. “Eh koma menene inma ni Agolace inada daraja sannan ina da tushe dama ni ban ɓoyewa cewa Agola bace Ni saboda idan kinga sunan su Amina da sunana kin san ba yar gidan bane, Ni sunana Khausar Usman Abubukar Lelewal sukuwa kinga ba haka sunan su yake ba daga nan ma mutum yasan Ni Agola ce ko dama anɓoye miki ne?”. Hannunta Hajiya Ruƙayya taja suka bar wajen zuwa gefe tace. “Khausar kifita har ƙansu kiyi abinda ke gabanki kinga duk yau baki samu karatu ba”. Kai Khausar ta gyaɗa mata sannan tayi mata Sallama ta tafi. Asma'u ce ta ƙaraso wajen Idanunta akan Samira da Abeeda dake zagin Khausar cikin yanayin sanyin muryanta tace. “Khausar kifita sabgar wa'annan yaran dan Allah keda su ba ɗaya bane kada ki ringa biye musu muta nen da ƙwaƙwalensu basa ja, kinga fa yanzu da ya kamata suna SS 3 nefa daƙiƙancinsa kesa kullum basa gaba sunan a jaɓe har muka isosu”. Yamutse fuska Khausar tayi kana tana matsa yatsun hannunta tace. “Kinsan Allah Asma'u Indai basu fita sabgata ba zan basu mamaki zan nuna musu Khausar Usman Abubakar Lelewal ba kanwar lasa bace”. Hannunta Asma'u ta riƙe tace. “Ni dai dan Allah ki fita sangarsu ai ko kare bai haushi shi kaɗai tukunna wai me kika yiwa Moddibo ya saki Punishment?”. Rau-rau da ido Khausar tayi sai kuma ta ya mutse fuska tare da jan tsaki kana tace. “Mutum yana nan kamar wani sabon boss sam fuskarsa babu fara'a yana nan sai baƙin mugunta. Kuma wallahi Wuta bal-bal ban yafe masa ba, ai bani kaɗai nayi kuskuren ba shima yayi yana tafiya kamar makaho, kuma yaseen saƙo na baki ki faɗa masa ehe”. Ta ida mgnar cike da tsiwa da murguɗa baki Asma'u kuwa dariyar dake cinta ta danne kana tace. “Aikuwa gashi nan abayanki yana ma jinki ba sai na faɗa masa ba”. Arazane Khausar ta saki ihu tare da rintse Idanunta cikin tsananin tsoro da rawan jiki ta juya tana mai faɗin. “Dan Allah! Dan Allah!! Dan Allah!!! kayi haƙuri Allah bada kai nake ba kuskuren harshene ni da kainama nakeyi”, Ta ida maganar tana buɗe Idanunta jin be tanka taba ga mamakinta bata gansa ba. Kallon Asma'u tayi wacce zuwa lokacin ta saki dariyar ta tace. “Fattanah sarkin tsiwa dama gwada ki nayi inga da gaske saƙon kika bani”. Harara Khausar ta zabga wa Asma'u amma batace Komai ba. Murmushi Asma'u tayi tare da jan hannunta zuwa resting chair dake cikin harabar makarantar suka zauna Asma'u ta fito da kula da ɗauke da pride rice da yaji kayan hadi da namar kaza suka ci. Bayan sun gama cin wannan Khausar ta buɗe bata kukan. Peper checking ne guzurin zabbin data dawo dasu. Sunaci suna ɗan hirarsu dai har suka gama, suka mike tare da zagaya classes din makarantar suna kallon yanda aka tsara makarantar kamar ba shiba. 12:10 suka koma aji. Bayan komawar su Malam Isa dake ɗaukar su Economist ya shiga ya koyar musu sosai Khausar da Asma'u ke fahimtar karatun 1:15 dai-dai suka fita sallah. Bayan sun fita Al'wala sukaje wajen da aka tanada dan alwala sukayi gefen maza da ban na mata da ban Amma masallacin guda daya ne saidai anraba daga tsakiya anyi katanga mata zasu shiga ta gefen dama maza tagefen hagu. Bayan sun idar da Sallah ƙarfe 1:30 suka koma aji wasu Malaman suka sake shiga. Sosai Malaman suka dage wajen koyar dasu domin anƙara musu Salarie sannan ankawo sabbin Malamai hakan yasa babu period din dake wucewa ba tare da anshiga ba 5:00 dai-dai suka tashi motar su Khausar tazo ta ɗauke su. Washe gari. Ma haka suka gudanar da karatunsu kamar na jiya. Acikin satin karatu suke gadan gadan babu kama ƙafar yaro saboda suna son dai-dai-ta komai na lokacin daya wuce ahutu koda wasa Khausar bata sake yin ganganci wani abu ya haɗa ta da Moddibo ba bare tayi masa laifi da zaran ya shiga ajinsu zata tattara duk kan nutsuwarta akansa tana sauraron abinda yake koyar musu kuma sosai take fahimta yayin da ita kuma Samira Sani zata tsaya aikin Kallonsa aduk sanda ya shiga musu shikuwa Moddibo duk yana lura da yanayin ko wannensu. Yau Alhamis ya kasance babu makaranta suna hutu. Khausar ce zaune a falon Mommy ta tana duba Mi'atu Hadith,Mommy dake Bedroom ta ƙwala mata kira Amsawa tayi tare da ajiye Hadith ta fita. Bakinta ɗauke da Sallama tashiga Bedroom din Kallonta Mommy tayi tace. “Khausar ɗibi wannan kayan ki kaiwa Hajiya Bunayya kala ɗaya nasiya mana”. Kallon mamaki Khausar ta yiwa Mommy anma wannan basabon abu bane ko yaushe Mommy na zaune zuciya ɗaya da ita tana kyautata mata, amma ita Hajiya Bunayya ba da zuciya ɗaya take zaune dasu ba. Gyaran Murya Mommy tayi tace. “Khausar tunanin me kike?” Murmushi Khausar tayi tare da ɗiban kayan tace. “Toh”,Mommy sannan ta fice. Bakinta ɗauke da Sallama ta shiga falon Hajiya Bunayya kana ta nemi waje ta zauna aɗaya daga cikin kujerun dake falon tace. “Ummah gashi Mommy na ta siya musu iri daya”. Washe baki Hajiya Bunayya tayi tare da kallon turamen Zannuwa da tsadaddun less ɗin tace. “Aaaa lalle kam Khausar Nagode Allah yayiwa ƙanwata al'barka muje inyi mata godiya”. Kai Khausar ta gyaɗa tare da miƙewa dai-dai lokacin Hajiya Lami mahaifiyar Samira Sani tayi sallama suka shigo atare. Kallon Khausar Hajiya tayi tace. “Khausar jeki nayi baƙi kice mata Nagode zan shigo anjima”. Kai Khausar ta gyaɗa tare da ficewa yayin da Samira ta bita da mugun kallo. Kallon Hajiya Lami Hajiya Bunayya tayi kana ta mika mata hannu suka tafa Dariyar ƙeta Hajiya Bunayya tayi tace. “Kalli Sokuwarki wai kaya ta saya mana iri ɗaya”. Dariya Hajiya Lami ta fashe dashi tare da cewa “Aaaa Ikon Allah sokuwa ta ƙarshen zamani kuwa wato hadda siya muku anko”. Tsaki Hajiya Bunayya tayi tace. “Bar ‘yar banza mai kama da ‘ya‘yan mayu tazo ta liƙewa mijina”. Hajiya Lami tace. “Aikam wa'annan mutanen sai Allah aike kika sake kika basu dama, kika bar mijinki ya ƙara aure ni yanzu Baban Samira ya isa yace zai ƙara aure ne, sannan bayan kin bari yayi auren ma kika barta tahaifi santalelen yaro me jikin girma bayan shi hadda ‘yan biyu da kawunansu kamar ‘Ya‘yan ruwa ga shegen gashi kamar ‘ya‘yan Aljanu”. Ƙwafa Hajiya Bunayya tayi kana tace. “Ai wallahi nayi sake amma daga ‘yan tagwayen babu ita ba sake haihuwa ina lura da ita kwannan kamar cikine da ita to bazan bari ta haife sa ba zanje wajen boka Kar'uzu azubar dama duk cikin ta uku kafin ’yan biyu ni nake sawa azubar shegiya ai bazan barta ba kenan yanzu ma inada niyya zanje wajenki jibi muje wajen Malami”. Gyara zama Hajiya Lami tayi tare da faɗin. “Aini ma abinda ya kawoni kenan Hajiya Bunayya in sanar miki”. Kallonta Hajiya Bunayya tayi tace. “Toh Meye faru?”. Ajiyar zuciya Hajiya Lami ta sauƙe tace. “Akwai wani Malami ne amakarantar su Samira take sonshi”. Cikin don jin ƙarshen zancen Hajiya Bunayya tace. “Toh wani Malami?”. “Wai shi malam Moddibo tana masifar sonshi shi kuma yana nan kamar Waliyi ko ta kanta bayayi”. “Ikon Allah”. Cewar Hajia Bunayya “Toh fa shine nake son zamu kai sunansa wajen Malami ya jawo mana hankalinsa da tunaninsa”. Jinjina kai Hajiya Bunayya tayi kana tace. “Eh hakan ma yayi shine dai-dai, gwara ajashi ya dawo yana binta, nima dama abinda zai kaini kenan harda batun Amina itama wani Malamin su take so”. Cikin mamaki Hajia Kamu tace. “Ita kuma wani Malamin take so?”. Da sauri Hajiya Bunayya tace. “Eh wani Malami take so wai shi M Jameel shi kuma baki ɗaya hankalinsa nakan wannan ‘yar matsiyatan!”. Cikin zato ido Hajiya Lami tace. “Wa kenan?". “Khausar mana”. Hajiya Lami kam baki ta saki tare da riƙe haɓa kana ta saki salati tace. “Ikon Allah Uwarta ta hanaki rawan gaban hantsi, sannan itama Khausar tun yanzu zata hana ‘yarki rawan gaban hantsi, ta hana ta samun abinda take so, to ko lallai kinada aiki ja a gabanki Yakamata muyi aggawan zuwa mu ɗauki mataki dan bata isa ba amma shi Jameel din ɗan gidan waye!?”. Murmushi Hajiya Bunayya tayi kana tace. “Ɗan gidan Alh Bashir Mafindi. Ko da yake yanzu anfi saninshi da Maidala ne”. Kai Hajiya Lami ta jinjina tace. “Kai-kai lallai kice babban kamu ne ina zamu yarda muyi wasa dashi waye bai san Alhaji Bashir Maidala ba” . “Ai dai kam ɗan masu kuɗi ina zamu bari muyi wasa da wannan damar tamu. Ai wlh koda zan tafi tsirara bazan taɓa bari ya auri Khausar ba, sannan Insha Allah zanyi kokarin ganin anja mana hankalinsa yaji ya tsaneta ya riƙa cin Ubanta kamar yanda Moddibo keyi mata amakaranta shine abinda yafi mana a'ala da kwanciyar hankali”. Acan waje kuwa Khausar ce tsaye aƙarshen Barandar Hajiya Bunayya cikin tarin al'ajabi da mamaki ta jinjina kanta bayan ta gama sauraron abinda suka faɗa.....! *GARKUWAR* taku ce dai MA'AURATA, da masu shirin aure, da masu jego, da yan gayu masu son k’amshi kece raini, da gyaran da zaike maimaita muku dararen forkon kuruciya* Ko kunsan Jikinmu na da sinadaran hormones da suke taimakawa dan’adam akan komai musamman lokacin da mace take mu’amalar aure da mijinta. Mafi akasari wannan hormones din ne ke samun matsala ko su yi sanyi koma su daina aiki kwata-kwata shi ne dalilin da zai sa mace tace bata jin sha’awa ko bata san dadin aure ba. Albishirinku ina da kayan da ke taimakawa wannan sinadaran du dawo aiki tukuru don karkato miki da kimarki wajan mai gida sannan su taimakawa wannan sinadaran hormones dinki su dinka secreting din ni’ima wadatacciya da zata taimaka miki ki gamsu mijinki ya gamsu fiye da tunaninki. Note: Kayana ba sa tsinka ruwan ni’ima suna dai taimakawa hormones dinki ne su tsattsafo da ni’imar musamman wacca cutar sanyi ko dattin mahaifa ya dankarar da su ya hana su yin aikinsu yanda ya kamata. Haka zalika idan kina da kyau ki kara da wanka. Zaki iya amfani da magani na na gargajiya wanda zai gyara miki sex hormones din kullum ki kasance cikin humidify wato cikin damshi mai albarka kamar yanda ake son mace. Yana gyara miki mara. Sai kamshi. Hajiyata daure ki fara amfani da turarena ki ji irin salon kamshin sa salo ne da zai daidaita ki da mijinki ya kankaro miki da kimarki a wajansa. Siyan na gari mayar da kudi gida. Ga masu buƙata ga number' wayata wanda nake whatsApp dashi 09097853276 kimin mgn ta whatsApp in har kin tabbatar kin shirya saya mu dai-dai ta, kayana ba ƙanana bane, shiyasa bana harkan karanta, muddin kinsan baki shirya sayaba Please kada kiyi min mgn ki bari sai kin shirya kuɗinki a hannu, ba ina nufin kayana bana talaka bane, no akwai ƙananan set na masu karamin karfi, banson aimin mgn a ɓatamin lokacin aiyukana a shirme baki shiryaba. Shine karantan da bana so. 0005388578 Jaiz bank AISHA GARKUWA ALIYU. In kin shirya ga number ta ga kuma account number ta wanda in mun gama mgn zaki turo kudin ki, kana insa miki Ka mota, duk ƙasar da kike kayana zaije gareki, amman fa in kinada dalilin zuwan nane🤝🏻sayan na gari meda kudi gida. GARKUWAR MA'AURATA By *GARKUWAR MARUBUTA* [19/07, 7:44 PM] Halimatu A/rahman Sadeeya: 📝🍇✨💫⏰🤴🏻👹❤️❤️❤️🍇 *SAKAYYAH* _Page10_ _NA_ *AYSHA ALIYU GARKUWA* 🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 *NA DAI FA KUSA GAMA FREE PAGE, SAURA KAƊAN. Yar uwa baki makara ba ki biya ki karanta cikin Aminci, littafin SAKAYYAH 1k ne kacal 0661110170 GTBank AISHA ALIYU GARKUWA sai ki turo min shaidar biyanki ta WHATSAPP 09097853276. Kana in saki a Groups ɗin dana buɗe na littafin SAKAYYAH wanda in dai ba a cikinsa kikeba toh yar uwa na sata kike gani. Amman na yanzu dai Free page ne* Ita kuwa Khausar Jinjina kanta tayi, yayin da idanunta ya cika da ruwan hawaye aranta tace. “Ta Allah bata ku ba amma kam yardan da Mommy na tayi miki ya ƙazanta ta gaza gane cewa ke ɗin kara da kiyashi ne ɗaukar rashin sani. Sai kuma ta juya cikin mutuwar jiki ta juya ta koma falon nasu bakinta ɗauke da Sallama. Zaune ta samu Mommy afalo Idanunta alumshe yayin da ta jingina bayanta da jikin kujeran. Ƙara sawa kusa da ita Khausar tayi tare da zama tace. “Mommy yadai baki shiga kichen ɗin ba?”. Ahankali Mommy ta ɓude Idanunta dake lumshe kana tace. “Wallahi Khausar bacci nake ji duk jikina babu ƙarfi!”. Jinjina Kai Khausar tayi cikin sanyu tace. “To kiyi baccin Mommy bari nashiga kichen nayi girkin”. Kai Mommy ta gyaɗa still Idanunta alumshe tace. “Toh”. Juyawa Khausar tayi ta shiga kichen ajikin sink din ta jingina asaman laɓɓanta tace. “Kenan yawan baccin da Mommy na keyi kwanan nan, ciki ne da ita wanda Hajiya Bunayya ke ƙoƙarin zubarwa”. A hankali ta saki Ajiyar zuciya da faɗin. “Allah mai iko”. Sai kuma ta juya ta ɗauki tukunya tasa ruwa ta ɗauraye cikin sannan ta tari ruwa da yawa aciki tarufe Sannan ta juya ta kunna Gas ta ɗaura ruwa, Jiki a mace ta buɗe drower Na'a na'a ta ɗiba tare da citta, kanamfari, da masoro kaɗan, gyara su tayi kana ta ɗaureyesu sannan ta saka cikin tukunyar. Doya ta ɗauko manya guda huɗu, ta fara ferewa. Hummmm taja sassayan numfashi lokacin da taji tea ɗin data ɗaura yanata baza ƙamshi alamun ya dafu, da sauri ta ƙarasa free doyan, kana ta wonkesu fes bayan ta rarraba su. Hannunta ta ɗauraye bayan ta stabtace wurin da ta feren. Flacks ta ɗauko guda huɗu cikasu tayi baki ɗaya, kana ta maidasu wurin zamansu. Wannan tukunyar ta kuma ɗaurayewa kana tasa ruwa ɗan madaidaici. Doyan ta ƙara sassarewa tayisu yan ma dai-dai-ta dai'dai sawa a baki, kana ta kuma wankewa ta tsanesu, kana ta juyeshi a tukunyar, gishiri ta ɗan tarfa a kai, sannan ta rufe tukunyar tare da ɗan dai-dai-ta wutan. Drower gefen dama ta ta kuma buɗe wa, wani farin roba ta jawo mai cike da ƙuli-ƙuli irin dogayen nan plate ta ɗauka saida ta cikashi kana ta maida ta rufe. Sannan ta ɗebi borkono dai-dai misali. Tasa a turmi kana ta sa kanamfari tare da Maggi star, Noo, Tera, Rayco, da dai sauransu, dakasu tayi , sannan tasa ƙaragon duk ta haɗa su ta dake su luƙui. Kana ta kwashesa a wasu ƴan robobi masu masifar kyau da yan marafensu guda huɗu. Fridge ɗin dake gefenta ta bude ta dauko goran ma shanu, ɗan wani tukunyan ƙasa ta ɗauka tare da tsulala manshanun, Daya gefen ta kunna gas ɗin, kana ta ɗaura, sai kuma ta ɗauki manyan albasa har guda huɗu, gyarasu tayi kana ta yayyankasu. Tukunyar da doyan ke ciki ta buɗe, Kai ta jinjina ganin ya kusa dafuwa, da sauri ta watsa rabin albasan da ta yanka ɗin a kai. Kana ta maida marfin ta rufe, tare da rage wutan. Ɗan ludayi, tasa cikin man shanun jin ya daina bada sauti alamun ruwan ciki ya ƙare, sake raba albasan biyu tayi ta watsashi cikin man shanun. Hhummmmmm taja wani dogon numfashi sabida wani irin masifeffen ƙamshi mai tsinka yawun mutun daya buɗe illahirin gidan. Kashe wutan babbar tukunyar tayi dan ya dafu albasar, ta razanu. Kana ta ɗauko kulli ta kwashe na sashin Hajia Bunayya tare dana Gimbiya Dadu. Sai kuma na Abbansu, Sannan na side dinsu. Sauƙe man tayi kana ta cire wannan albasan daya fara ƙonewa, sai kuma ta juye wannan sauran, shuyuuuu ya bada sautin soyuwa da zafin man. ɗaya daga cikin manyan ƙullin naman dake cikin fridge ta ɗauka mai sokoki zalla anyi ta kansu dogo-dogo. Ɗaurayewa tayi tasa a yar madaidaicin tukunya ta zuba naman, dama already ta jajjaga ɗanyen citta da tafarnuwa ta buɗe ta zuba aciki sannan ta Marmasa Maggi da time kana ta jajjaga attaruhu da albasa ta zuba tare da diban man shanun data soya ta watsa a ciki da duk sauran spices,Cikin Mintuna kaɗan kichen ɗin ya ɗauki mayataccen ƙamshin girkin dana man shanu daya wadata aciki zazzafan gashin da takeyiwa Abban. Mommy kuwa ahankali ta miƙe tashiga kichen ɗin Idanunta akan Khausar dake wanke yan kwanunkan data ɓata, cikin alamun bacci tace. “Ƙamshin girkin ki ne ya tasheni da gaba baccin. nazo in tayaki gashi kuma naga kamar ma kin gama”. Murmushi Khausar tayi tana motsa gashin naman mai romon da takeyi wanda tuni yanata ɓararraka kai ta jinjina kana tace. “Mommy kije ki huta nama gama fa”. Murmushi Mommy tayi kana tace. “A'a kada ki damu ai baccin ya sakeni”. Kai kawai Khausar ta gyaɗa sannan ta cigaba da aikinta tana sauƙe gashin Mommy ta taimaka mata suka juye kulan Abba da kuma na Dadu, saura kuma suka sawa Hajia Bunayya saura kuma suka barwa kansu. “Yauwa ɗauki na Ummanki ki kai mata”. cewar Mommy, cikin sauƙe numfashi Khausar ta ɗauka bayan ta sa jera yan robobin man shanun da yajin ƙuli-ƙulin, sai yar kulan gashin naman. Kana ta nufi sashen bakinta ɗauke da sallama tashiga. Amina dake zaune riƙe da waya ahannu ta watsa mata kallon tsana batare data amsa sallamar taba tace. “Agola kin zo kina wani tunƙaho kamar gidan tsohonki ne Masarautar very soon zaki bar gidan nan dan nafi ƙarfin nayi shearing abinda nake so dake”. Ya mutsa fuska Khausar tayi tare da jan siririn tsaki tace. “Iska na wahalar dame kayan kara wannan ƴar masarautar kike mgn a kai har wata siyace”. tana ida maganar ta fice batare data jira jin abinda Amina zata ceba. Kai tsaye kichen ta nufa tsaye ta samu Mommy tana ɗauraye tukwanen da Khausar tayi amfani dashi kallon ta tayi tace. “Ki ɗauki kular Gimbiya Dadu ki kai mata”. Langwaɓar da kai Khausar tayi tace. “Ayyah Mommy Haiydar ya Kai mana”. Juyawa Mommy tayi ta kalleta da faɗin. “Wai Khausar Meyesa idan na aike ki sashen Gimbiya Dadu sai kice in aiki Haiydar bana jin daɗin abinda kike min fa wato kina nuna min cewa ke ba jikarta bace?”. Girgiza kai Khausar tayi tace. “Wallahi Mommy Ina tsoron zuwa wajenta bana shiri da ita”. Kallon Mamaki Mommy tayi mata kafin ta watsa mata harara da faɗin. “Rufe min baki zakiji tsoronta ita ɗin kurace? wato kinje kakar ki tasa Miki ra'ayi da batun cewa ita Mayya ce da sauransu ko?”. Girgiza kai Khausar tayi Idanunta cike da ruwan hawaye aranta tace. har yanzu Mommy ba zata gane ba taya zan ganar da ita cewa ni kaina na gamsu da cewa matar nan Mayya ce. Amma nasan kona faɗa ba zata yarda ba dan yanda take haƙiƙan cewa akan ba Mayya bace ko ‘ya‘yan cikinta basa haƙiƙan cewa akan hakan, ita babu dama ace Gimbiya Dadu Mayya ce bayan ni da kaina naga alamomin hakan kuma ya fito da bakinta ta faɗa min ita Mayyace kawai ya rage amma sam Mommy taƙi yarda idan taji mutum ya fadawa Gimbiya Dadu Mayya aita bala'i da ita se kace Uwarta aka kira Mayya. Ita kuwa Mommy ganin yanda Khausar ta tsirawa waje ɗaya idanu yasa aɗan fusace tace. “Khausar ba magana nake Miki ba ko baza kije bane Inje da kaina?!”. Asanyaye tace. “Ayyah Mommy kiyi haƙuri zanje”. Ta Faɗa tare da ɗaukar kulan ta fice tana furta. ”اعذبكلمتلله تممت منشررم حلق“. Bakinta ɗauke da Sallama tashiga falon akan darduma taga Gimbiya Dadu na sallar maghariba cikin sauri ta ajiye kular. Ita kuwa Gimbiya jin Muryan Khausar yasa cikin hanzari tayi sallama batare data idar ba ta juya ta zuba mata Na mujiya. Ita kuwa Khausar cikin sauri ta juya ta fice daga sashen ta nufi sashen su tana sakin Ajiyar zuciya sai kuma ta furta. “Alhamdulillah”. Sosai tayi farin cikin tarar da Gimbiya Dadu tana Sallah. Koda ta shiga Falon nasu bata samu Mommy ba da alama tana ciki tana sallah kai tsaye Bedroom ɗin su ta wuce tare da shiga toilet bayan tayi addu'a. Anutse tayi alwala tare da fitowa da ƙafar dama. Darduma mai taushi dake fitar da sanyayyan ƙamshi ta shimfiɗa kana ta sanya dogon hijabinta ta fuskanci alƙibla cikin nutsuwa tare da maida komai zuwa ga mahalicci ta gabatar da sallah bayan ta idar ta ɗaga hannunta biyu sama tare da lumshe Idanunta cikin tsantsar nutsuwa tare da ladabi alokacin neman wani buƙata ga Ubangiji mabuwayi gagara Misali ta ɗaga hannunta biyu tace. “Ya waduud,Ya zul'arshil Majeed,Ya fa'alil lima yureed As'aluka bi izzatil lati la yura wa mulki kallazi la yurad wa nuru wajihikallazi mala alkana arshik najjini min hazal mujrimin ya Allah ka tsare min mahaifiyata da abinda ke cikinta daga sharrin Mai sharri”. ta faɗa tare da shafawa Alkur'ani ta ɗauka ta fara Muraja'a tun daga Kahf sai data je Hajj kafin ta tsaya ta miƙe ta ida da Isha'i awajen ta kishingiɗa da haka bacci ya ɗauke ta. Washe gari juma'a Khausar na zauna afalon Mommy akan Lallausan Capet yayin da Mommy ke saman kujera Khausar na matsa mata ƙafafunta ahankali Khausar ta ɗago kai tare da kallon Mommy da Idanunta ke lumshe tace. “Mommy wallahi nayi missing Hajja Nana, Baffa Jauro Sadik, Dije duka mutanen Rugar ma nayi kewarsu gashi babu network bare nakira naji Muryansa”. Murmushi Mommy tayi tare da jan numfashi kana ta buɗe Idanunta dake lumshe tace. “Lalle kam Khausar yau kece ke faɗin Kinyi kewar Hajja Nana da bakin ki?”. Murmushi Khausar tayi wanda ya lotsar da dimple ɗin ta kana tana cigaba da yiwa Mommy massaging ƙafafunta tace. “Allah tana da daɗin zama kawai dai faɗanta da kuma mulkin mallaka da take nunawa yasa bamu jituwa amma tanason Babana da yawa sannan tana masa addu'a ni kuwa kinga duk mai yiwa Babana addu'a ina ƙaunarsa”. Ta ƙarashe tare da buɗe Idanunta dake lumshe wanda ruwan hawaye ya cika su. Shafa kanta Mommy tayi tare tace. “Ubangiji Allah yajiƙan sa da rahma Allah ya gafarta masa Ubangiji ya jiƙan dukkan musulman da suka rigamu gidan gaskiya”. Sanyayyar Ajiyar zuciya me haɗe da kyewa Khausar ta saki kana ahankali ta furta. “Ameen”. Mommy tace. “Sai ki shirya idan kunyi wani hutun kije ki gansu”. Wara ido Khausar tayi tare da gyara zamanta kana fuskarta ɗauke da murmushi tace. “Ai lalle kam”. Sai kuma tayi saurin juyawa jin Muryan Asma'u na sallama. Ƙarasawa Falon Asma'u tayi tare da zama daga gefen hagun Khausar ta ajiye Handbag dake hannunta ta shiga Matsawa Mommy ƙafanta na hagu da faɗin. “Mommy ina kwana yasu Raudat?”. Hannu Mommy ta sanya ta shafa kanta da faɗin. “Lafiya lau Asma'u ya gida yasu Umminki?”. Asma'u na cigaba da Matsawa Mommy ƙafanta tace. “Tana lafiya tace na gaisheki”. Mommy tace. “Ina amsawa”. Ita kuwa khausar kallon Asma'u tayi tace. “Sannu da zuwa taso mu shiga ciki”. Kai Asma'u ta gyaɗa sannan ta miƙe ta ɗauki Handbag ɗin ta suka shiga. Zama tayi agefen gadon Idanunta akan Khausar data buɗe ƙaramin fridge ta ɗebo mata kayan marmari tace. “Anbani saƙon gaisuwa in kawo miki”. Ajiye ƙaramin Plate ɗin Khausar tayi tare da zama tace. “Toh ina Amsawa wani bawan Allah ne?”. Da sauri Asma'u ta ƙumshe dariyar dake cikinta kana tace. “Moddibo ne yace agaisheki da hannu”. Zare idanu Khausar tayi lokaci ɗaya ta ƙware da Inabi dake bakinta da dugu ta miƙe ta nufi fridge ta ɓude Goran Swan water ta ɓude ta kafa abakinta saida tasha fiye da rabi kafin ta janye roban daga bakinta tana maida numfashi. Asma'u kuwa kasa riƙe dariyar ta tayi cikin dariya sosai tace. “Me haka Khausar daga jin sunan Moddibo zaki wani ruɗe haka?,sai kace wani abin tsoro!?”. Zama Khausar tayi tana maida numfashi tace. “Wallahi mutumin nan ya wuce inda kike tunani yanda kika san bashida zuciya aƙirjinsa baya jin bada haƙuri fa”. Ta ida maganar tare da jan siririn tsaki tana tuno fuskar Moddibo lokacin da take bashi haƙuri. Asma'u ta katse shirun tare da buɗe Handbag ɗin ta ta ciro takardan Economics da Mi'atu Hadith da sauran darasin da sukayi ta miƙa mata tace. “Gashi ki kwafa sannan kiyi karatu akai”. Amsa Khausar tayi tare da budewa tace. “Toh shikenan ba matsala zan duba”. Bayan sun sake taɓa hira Asma'u tace. “Zan tafi”. Khausar tace. “Tun yanzu?”. Hararanta Asma'u tayi tayi tace. “Eyyyyy lalle kam aigwara ni dakeke sai ki kusan shekara bakije gidanmu ba”. Tana gama Fadar haka ta Miƙe ta fita. Dariya Khausar tayi tare da sanya Blue Black ɗin hijabinta ta fice afalon ta samu Asma'u nayiwa Mommy Sallama bayanta tabi suka fice. Washe gari ta kama ranar. Asabar Hajiya Bunayya da Hajiya Lami ce acikin mota, suka nufi unguwar shamaƙi, yayin da Hajiya Bunayya ke tuƙi suna sauraron wakar Nazeer Sarkin Waƙa mai taken Bamu babu ku,kuma baku babu mu. Cike da nishaɗi Hajiya Lami tace. “Hajiya Bunayya Matsalar mu tazo ƙarshe da zaran munje wajen wannan mutumin komai yazo ƙarshe dan ina da tabbacin aikinsa”. Dariya Hajiya Bunayya ta sheƙe dashi tare da buga stairing motar tace. “Kedai bari nayi al'ƙawari saina tarwatsa wannan matar”. Da wannan hiran suka isa unguwar daga can bakin hanya sukayi parking motarsu. Kana suka ɗanyi tafiyar ƙafa kaɗan suka tsallaka titin, suka nufi wani ƙaton kango mai zagaye da dogon katanga da duhuwar bishiyoyi, da baya-baya suka fara shiga cikin wajen da manyan bishiyoyin Tsamiya dana kuka suka masa ƙawanya sai kuma wasu manyan bishiyoyi irin na Ceɗiya masu masifar tsawo da duhu kana sai wani ƙaramin bukka daya kasance Atsakiyar bishiyoyin, jikin bukkar ke waye yake da jajayen ƙyalle da wasu irin ƙwarya masu masifar munin gani ajikin ƙwaryan akwai kuratandu sai kuma wasu baƙaƙen ƙaho masu siffar fuskan bil Adam. Daga nesa suka ajiye takalmansu kana suka cigaba da tafiya da baya har suka shiga cikin gidan da ƙafar hagu yayinda wani masifaffen ɗoyi ya cika gidan baki daya ya mamaye ilahirin gidan. Cikin ɗaga sautin murya suka haɗa baki wajen faɗin". “An gaida Boka Kar'uzu uban bokaye angaida la'anannen Uban la'anannu mugu uban mugaye Hatsabibi uban hatsabibai”. Daga ciki kuwa wata daskararriyar murya mai firgitarwa mara daɗin saurara yace. “Kushigo da baya-baya kana ku tabbata ƙafar hagu zaku riƙa takawa har ku iso gareni”. Cikin tsinkewar zuciya da matsanancin tsoron kada su saɓa masa doka cike da biyayya suka gyaɗa masa kai tare da ƙara sawa kusa dashi suka zauna suna maida numfashi. Cikin daskararriyar muryarsa mara daɗin sauraro yace. “Ku tashi anan suna zaune zaku danne ɗan ƙundalo mai ido agoshi! Maza ku koma ta gefen hagu bana ƙaunar ganin ku. A dama saboda ba aikin dama zamu yiba”. Tsaban tsoro saidai Hajiya Bunayya ta dungura tare da kurje hannunta kana jikinsu na rawa suka koma gefen hagunsa. Kallon Hajiya Bunayya yayi ya kece da wata mahaukaciyar dariya me tsananin razanarwa, ya nunata da wani mummunan yatsansa da farce yayi tsawo kana yace. “Kin makara cikinta har ya kusa wata uku amma zamu jijjigesa da ƙarfin ikon mu zamu fito dashi!”. Ita kuwa Hajiya Bunayya Atake taji tsoron ta ya tafi ta washe baki da faɗin. “Laaa Malam kasan abinda ke tafe dani?”. Cikin fushi yace. “Sunana ba Malam ba Kur'ani kika gani agabana ko hadisai da za ki kirani da Malam ki kirani da Boka Kar'uzu uban bokaye La'anannen uban la'anannu Mugu Uban Mugaye”. Ƙasa da kai tayi tana cewa. “Tuba nake Boka Kar'uzu bazan sake ba”. Kai ya gyaɗa mata yace. “Sai kuma batun Jameel da ’yarki Amina” Cikin rawan jiki tace. “Eh boka Kar'uzu”. Ya kece da wata mahaukaciyar dariya yace. “Ai ƙaddarar abai-bai take,Ai ƙaddarar abai-bai take, ƙaddarar abai-bai take!”. Ita kuwa Hajiya Lami cikin zaƙuwa take gyaɗa kai. Hajiya Bunayya tace. “Boka kamar ya ƙaddara abai-bai take ban fahimta ba”. Yace. “Babu damuwa za'ayi Miki aiki”. Hajiya Lami ta gyara zama sosai tace. “Toh Boka Kar'uzu ni ya batun ‘yata?”. Ya sake kecewa da wata mahaukaciyar dariya yace. “Aike batun ki mai sauƙi ne shi wannan babu wata Aransa shi wannan dakike gani yana nan kamar Waliyi ne, koko ince katako, sai dai fa akwai ganye bishiya da yake tsirowa ajikinsa har ta fara jijiya ajikinsa tana gab da zuba rassuna”. Hajiya Lami tace. “Boka koma wani irin ganye ne Indai bana Samira bace atun ɓukesa”. Kai ya gyaɗa kana yace. “Angama angama”. Cikin jin dadi ta juya ta kalli Hajiya Bunayya tana sakar mata da murmushi alamar da akwai Nasara. Sai kuma ta juya ta kalli Boka Kar'uzu tace. “Ya batun abubuwan aiki?”. A tsawace boka Kar'uzu yace. “Zaku kawo Fararen Bunsuraye guda uku, Da baƙaken karnuka guda biyu da baƙar kaza mai bungi-bungi guda ɗaya na batun aikin zubar da ciki. Batun Jameel kuwa zaki kawo gurguwar jaka mace sannan ki samu makauniyar tinkiya me watanni bakwai sai kuma agwagwa fara mai ƙafa ɗaya”. Zare Idanu sukayi Atsorace jin abubuwan da ake buƙata. Ya cigaba da cewa. “Batun aikin Moddibo kuwa zaku kawo Gurguwar shanu ja mai Ido ɗaya da kuma namijin doki fari soll wanda aka haifesa acikin gida sai kuma ku samo Alade guda biyu mace dana miji”. Cikin tashin hankali da damuwa Hajiya Lami tace. “Boka a ina zamu iya samo wa'annan abubuwan aise kai saidai mu bayar asamo”. Yace. “Toh ku ajiye kuɗin masu tarin yawa”. Cikin rawan jiki Hajiya Bunayya tasa hannu a jakarta ta ciro kuɗi wanda batasan adadin suba ta ajiye masa”. Kallon kuɗin yayi yace. “Kuje bayan sati biyu kuzo ku karɓi kayan aikinku sha yanzu magani yanzu”. Godiya suka masa kana suka tashi suka fita kamar yanda suka shigo. Acan ɓangaren su Khausar kuwa karatu suke sosai babu kama ƙafar yaro sabbin Malamai da aka kawo musu sun zage damtse wajen koyar da ɗalibai ga kuma sabbin ɗalibai da ake shigowa dasu saboda yanda aka tsara Makarantar sosai makarantar ya sake samun ɗaukaka fiye da farko ga kuma shirye-shiryen musabaƙa da akeyi na Jahar Taraba baki ɗaya Khausar da Asma'u sun sake dagewa. Bayan sati biyu Hajiya Bunayya da Hajiya Lami ce zaune agaban Boka Kar'uzu. Wani ƙullin magani ya ɗauka tare da kallon Hajiya Bunayya ya miƙa mata kana yace. “Wannan ki dafa shi da farfesun kayan ciki ki bawa Hajiya Aysha tana ciki, sunan cikinta anyi angama saide wani cikin bashi ba!. Sannan idan kin shirya kizo za'a zazzage mata mahaifa asa mata ajiya yanda baza ta sake ɗaukar wani cikin ba, sannan kuma mijinta zai tsaneta ba zai sake sha'awar kusantar taba!”. Murmushin samun nasara Hajiya Bunayya tayi tace. “Boka Indai cikin nan ya zube zan dawo akan aikin amma yanzu burina cikin ya zube sannan ajawo hankalin Jameel kan Amina”. Wata mahaukaciyar dariya Boka Kar'uzu ya sheƙe dashi yace. “Ga wannan”. Hannu bibbiyu Hajiya Bunayya tasa amshi ƙullin maganin tana jujjuyawa yace. “Ki bawa ‘Yarki Amina tayi wanka dashi sannan tayi hayaƙi idan zatayi hayaƙin ta ɗago kaskon ta kawo bakinta ta riƙa kiran Jameel!, Jameel!!, Jameel!!! na tsawon kwanaki uku sannan ta tsallake kwana uku ta sake na kwana uku na sannan ta sake kwana uku ta tsallake kwana uku sannan ta sake kwana uku kuma ko wanne idan tazo hayaƙin sai takai kaskon bakinta ta kira sunansa kada ku yarda asamu kuskure dan in an fa samu kuskure abun bazaiyi kyau ba”. Kallon Hajiya Lami Hajiya Bunayya tayi tare da jinjina mata hannu tana murmushi cikin ƙasa da murya tace. “Alhamdulillah nakusa ganin ƙarshen wannan matsiyatan”. Martanin Murmushin Hajiya Lami ta mata itama ranta fess burinsu ya kusa cika. Tunda Boka Kar'uzu yace. “Muddin tayi na tsawon wannan kwanakin shida kansa zai kawo kansa gareta idan kuma wannan baiyi ba akwai wanda zamu sakeyi saidai shi wannan kankat ne amma shi sai farkon damuna tukunna zamu samu ayishi”. Cike da farin ciki Hajiya Bunayya tace. “Boka Kar'uzu Uban bokaye Insha Allahu ma nasan wannan aikin zaici”. Cikin wata razananniyar tsawa yace. “Oho Ni dai nace kada ki sake kiramin sunan Allah anan domin da kina jin tsoronsa ba zaki zo nanba bare har kinemi aikata mugun abu akan wani idan kuma kina son aikin ki ya ɓaci ki sake kiran Allah anan”. Cikin rawan baki da tsoron kada aikinta yaƙi ci tace. “Tuba nake Boka Kar'uzu Uban bokaye La'anannen Uban La'anannu Mugu Uban mugaye da ikon ka wannan aiki zaici”. Ya sheƙe da wata mahaukaciyar dariya mai kama da sautin ƙaran lalataccen Injin Markaɗe yace. “Yanzu ne aikin ki zaiyi yanzu ne kika yi magana mai ma'ana”. Ta saki ajiyar zuciya cike da farin ciki. Hajiya Lami ta matso kusa tare da gyara zama sosai tana fuskantar Boka tace. “Ni kuma ya maganar ’yata?”. Wani irin kallo ya mata kana yace. “Na ‘yarki sai anyi babban shiri domin wannan da kike gani shida saƙago basu da banbanci baya kallon mace ako wani irin mataki daya wuce ɗaliba ya karantar da ita ya kuma bata ilimi da tarbiyya shi koda mace zata wuce tsirara agabansa babu abinda zai damesa da ita tamkar zuciyar dutse ne aƙirjinsa!”. Ta gumi Hajiya Lami tayi tare da faɗin. “Ikon Allah aƙasan ranta”. Boka Kar'uzu ya cigaba da cewa. “Sai munyi mata shiri sosai yanda lokaci ɗaya zata jawo hankalin sa gareta sai bayan wata biyu zaki zo ki karɓi haɗin da muke tsuma shi sannan tayi kokari ta bashi yaci daya ci aiki ya gama”. Ajiyar zuciya Hajiya Lami ta saki tace. “Da ƙarfin ikon ka zamuyi hakan boka”. Ya kece da wata mahaukaciyar dare yace. “Na gama daku zaku iya tafiya”. Miƙewa sukayi suka ce. “Godiya muke Boka Kar'uzu Uban bokaye La'anannen Uban La'anannu Mugu Uban mugaye”. Shikuwa Dariya ya kece dashi yana jin daɗin kirarin da ake masa kamar yanda suka saba shiga haka suka fita da baya. Cikin tsananin farin ciki Amina ke kallon Hajiya Bunayya dake mata bayani karɓan maganin tayi tare da rungume Hajiya Bunayya tace. “Nagode Umma”. Ƙullin maganin ta karɓa sannan ta shiga ban ɗaki tayi wanka dashi tana fitowa Hajiya Bunayya ta kawo mata wuta akasko ta bata zama Amina tayi tare da kai saitin kaskon bakinta tace. “Jameel!, Jameel!!, Jameel!!!”. Ta faɗa da ƙarfi yayin da hayaƙin ke bin ilahirin jikinta kallon Hajiya Bunayya tayi cikin jin daɗi tace. “Umma M Jameel ya Kusa zama mallakina?”. Dariya Hajiya Bunayya tayi tace. “Ƙwarai kuwa?”. Asiya ce tashigo falon da Sallama da sauri ta toshe hancinta jin wani masifaffen wari da ƙauri tayi saurin kallon ƙofar Bedroom ɗin Hajiya Bunayya inda nan take jin wari da ƙaurin ke fita. Tana ƙoƙarin shiga Hajiya Bunayya ta fito Kallonta Asiya tayi tace. “Ummah warin meke fita daga ɗakinki?”. Harara Hajiya Bunayya ta watsa mata tace. “Warin lafiya ko kuma ke ki kafi kowa hanci?”. Girgiza kai Asiya tayi tace. “Wallahi Ummah da gaske akwai..”. Tsawa Hajiya Bunayya ta buga mata da faɗin. “Ki wuce kibani waje sakaryar banza mara tunani”. Ahankali Asiya tace. “Allah yabaki haƙuri Ummah”. Kana ta juya cikin mutuwar jiki ta nufi ɗakinta. Bayan wata ɗaya: Amina ta gama amfani da duk maganin da Hajiya Bunayya ta karɓo mata awajen Boka Kar'uzu cike da farin ciki ta dubi Hajiya Bunayya asanda take sanya uniform ɗinta tace. “Ummah na matsu na isa Makaranta inga irin tarban da Jameel zai min!”. Murmushi Hajiya Bunayya tayi da faɗin. “Kede ki kama kanki karki bari ya gane kina sonshi ya rainaki dan yanzu sai yanda mukayi dashi”. Asiya data fito daga kichen hannunta riƙe da Cup ɗin tea dake tururi ta zauna akan ɗaya daga cikin kujerun falon Idanunta akan Amina tace. “Amina ki maida hankali akan karatunki kada kice zakiyi wasa da damarki komai da kika gani arayuwa muƙaddari ne daga Ubangiji”. Cikin tsawa Hajiya Bunayya tace. “Asiya zanci Ubanki fa idan baki fita sabgar Amina ba shegiyar yarinya me baƙin halin tsiya. Niko anya ma ba canza min ke akayi ba, dan wallahi badan kamannin dake tsakanin mu ba sai ince sauya min ke akayi”. Miƙewa Asiya tayi tace. “Allah ya baki haƙuri Umma amma ita gaskiya ɗaya ce”. Harara Amina ta watsa mata tace. “Ke har wani gaskiya ce dake to ki riƙe gaskiyar ki bama bukata”. tana gama fadar haka ta fice. Atare suka fito da Khausar dake riƙe da hannun Raudat kallo ɗaya Khausar ta mata ta kawar da kanta gefe, Ita kuwa Amina murmushi mai cike da ma'anoni ta sakarwa Khausar sannan tashiga motar yayin da Khausar tabi bayan ta suka shiga sannan driver yaja motar suka tafi. Motar na tsayawa kowa ya nufi ajinsu kamar kullum saida Khausar takai Raudat ajinsu kafin ta wuce ajinsu. Aɓangaren Amina kuwa kai tsaye ajinsu ta nufa tare da zama tana sakin murmushi duk da Amina da Khausar Shigansu baa daɗewa M Jameel ya shigo ajin cikin wata farar gezner me kyau yayin da kansa ke sanye da baƙin hula gashinsa ya fito ta ƙeya ƙafarsa sanye da sau ciki baƙi jikinsa na fitar da sanyayyan ƙamshi Amina kuwa ta gumi tayi tare da zu bawa sajensa zuwa gemunsa idanu tana mai furta. “Wowww”. Shi kuwa M Jameel hankalinsa ya mayar kan Black Board. Cikin karya murya tare da lanƙwasa harshe Amina tace. “Malam Barka da safiya”. Anutse M Jameel ya juya ya kalleta cikin sauri ya runtse Idanunsa da ƙarfin gaske. Sai kuma ya sake buɗewa akan fuskarta still da sauri ya sake runtse Idanunsa yana mai furta. “Hasbunallahu wani'imal wakil. Astagfirullah wa'atubu ilaik”. Ita kuwa Amina cike da ƙissa ta sake karya harshe tana juya Idanunta tace. “Malam ina kwana”. Shi kuwa M Jameel Batare daya juya ya kalleta ba ya ɗaga mata hannu, domin tun sanda ya kalli fuskarta sau ɗaya yaga kamar an ƙona fuskar Biri, sosai ta masa muni tunda yake kallon fuskar yarinyar bai taɓa ganin tayi masa muni irin na yau ba, baki ɗaya fuskarta babu haske bare annuri Kawar da kansa yayi ya cigaba da koyar wansa batare daya yarda ya sake kollon inda take ba har yagama ya fita. Ita kuwa Amina bata kawo komai aranta ba domin atunaninta maganin ne ya fara aiki. Acan ajinsu Khausar kuwa Moddibo ne tsaye jikin Black Board Ya rubuta Geography ajiki, Da alama shine subject ɗin da zai riƙa ɗaukansu. Jikinsa sanye da Jallabiya Coffee color yayin da kansa ke naɗe da hirami siririn sajensa zuwa gemunsa yasha gyara sai sheƙi yake jikinsa na fitar da sanyayyan ƙamshi tularen Oud. Cikin nutsuwa da kuma sanyin Muryansa ya gyara tsayuwar sa tare da harɗe hannayensa aƙirji kana ya ɗan lumshe idanunsa kafin yace. “Class What is Geogry?”. ya ƙare tambayar cikin tsananin tsuke fuska da tsare hirar samata ƙasa, sabida yanayin dariasin in yayi garaje yara zasu rainasa, Allah ya sani ba ƙaunar darasin yakeba sabida yanayin abubuwan dake ƙunshe a ciki masu cin karo da addini. Shiru class din yayi ba wanda yayi magana sabida yadda baya kallon idonsu haka suna kan suke shayin koda motsi bare Kallonsa. Khausar da Idanunta ke lumshe ta buɗe tare da zaro harshe ta ɗan lashi lips ɗin ta sai kuma ahankali ta ɗaga siririn hannunta dake maƙale da zoben azurfa da kuma Gold. Shi kuwa Moddibo ahankali ya maida da idanunsa zuwa ta inda take. Kana tsare sashin da taken yayi da ido amman ba fuskantar yake kalloba, ƙara tsuke fuska yayi tare da sa hannunsa ya shafa yalwataccen sajen dake fuskarsa kana ya mata alamun ta tashi. Cikin nutsuwa tare da taka tsan-tsan akan gudun lefin da zatayi ta motsa lips ɗin ta da yayi pich saboda man baki data shafa kana ta lumshe Idanunta tace. “Geography can be defined as the discription of the Earth”. Jinjina kai Moddibo yayi tare da faɗin. “Dayyit, sit-down”. Kai ta gyaɗa tare da zama. Ahankali ya motsa lips ɗinsa da faɗin. "Yah Salam". Yayi mgnar yadda ba mai jinshi. gajeren tsaki, Samira Sani taja dan ji tayi kamar ta haɗiyi zuciya ta mutu saboda baƙin ciki taso ace itace zatayi wannan karatun Shikuwa Moddibo kallon Khausar yayi tare da yimata alamar tazo cikin sauri ta miƙe ta isa gabansa, ba tare da yace mata komai baya miƙa mata hannunsa. Kallon tattausan farin tafin hannunsa dake ɗauke da zara-zaran yatsu da ga wasu zoben azurfa fari da baki daya ƙawata yatsun. Cikin rawan murya tace. “Malam mai zanyi?”. Ya mutsa fuska yayi tare da watsa mata harara daya sa ‘ya‘yan hanjinta kaɗawa da ido ya nuna mata zobunan hannunta. Cikin rawan jiki ta cire ta basa lokaci ɗaya Idanunta suka sauya launi sosai take masifar son zoben ɗaya Mommy tace ta bata ɗaya kuma Hajja Nana ce ta bata ta kuma shaida mata tun na babantane na azurfan. Saida ta koma ta zauna yace. “Nasha faɗa muku cewa nan ba wajen ado bane idan kowa yace zaiyi ado yazo ai wasu ma baza agansu ba”. Ya ida maganar tare da juyawa ya cigaba da koyar musu cike da ƙwarewa tare da kare ƙa'idar musulunci gudun dulmuyar tunanin ɗalibai. Bayan kwana uku baki daya Amina tashiga damuwa da tashin hankali koda ta gaida M Jameel baya Amsawa sai dai ya ɗaga mata hannu, gwara ma da yana kallonta Sannan wataran yakan mata murmushi amma yanzu koda kallonta baya ƙaunar yi. Bayan antashi tana komawa gida. Kai tsaye Bedroom din Hajiya Bunayya ta nufa. Zaune ta samu Hajiya Bunayya riƙe da kofin tea mai ɗumi ahannunta. Zama tayi agefen Hajiya Bunayya cikin raunin murya tace. “Ummah tunda fa nagama aiki da maganin M Jameel Koda kallona ne baya ƙaunaryi, ko gaishesa nayi saidai ya ɗaga min hannun!”. Da Mamaki Hajiya Bunayya tace. “Ikon Allah to ya zama dole inshirya na koma gidan Boka Kar'uzu inji me yesa”. Gyaɗa kai Amina tayi tace. “Gaskiya ya kamata dai Ummah". Hajiya Bunayya tace. “Gashi nima yau nakeso in fara na wannan matsiyaciyar matar dan nafi so dama sai kin gama naki sai in dafa in bata”. Amina tace. “Ya kamata dai kam yazo tana ta cika mana gida da yara”. Ita kuwa Hajiya Bunayya miƙewa tayi da kanta ta shiga kichen ta buɗe fridge ta ɗauko kayan ciki ta haɗa masa kayan ƙamshi da kayan hadi Sosai sai tashin ƙamshi yake. Warmers ta ɗauka ta juye kana ta dauko ƙullin maganin da boka Kar'uzu ya bata ta barbaɗa akai sannan ta ɗauka ta nufi sashen Hajiya Aysha dashi. Mommy na zaune afalo ta miƙe ƙafafunta ta jiyo Sallamar Hajiya Bunayya murmushi tayi tare da tace. “Yaya kece da kanki sannu da zuwa”. Murmushi Hajiya Bunayya tayi tace. “Wallahi kuwa kinga Perpesoup nayi na kayan ciki, nasan kuma kina so, shiyasa nace nari na kawo miki, idan kinsha da dan ruwan Tea mai ɗumi zakaji daɗi asanyin da ake”. Murmushi Mommy tayi tace. “Aikuwa Nagode yanzu nake tunanin tashi in dafa ko indomie ne naci dan na gagara cin tuwon". Murmushi Hajiya Bunayya tayi tace. “Ayyah ƙanwata to ga wannan sai kisha ai zakiji daɗinsa”. Acan ɗaki kuwa Khausar ce tsaye jikin wodurobe tana gyara kayansu da Raudat ta burkitasu. Siririn tsaki ta saki tare da kallon tulin kayansu dake burkice kamar basu taɓa ganin ninkiba bare guga stool taja ta zauna tana ninke kayan. Acan falo kuwa yunƙurawa Mommy tayi da faɗin. “Bari na ɗauko Plate". Da sauri Hajiya Bunayya ta mike tare da cewa. “A'a bari na ɗauko Miki”. Ta Faɗa tare da shiga kichen ɗin. Ita kuwa Mommy murmushi tayi aranta tana jinjinawa ƙaunar da Hajiya Bunayya ke nuna mata tabbas samun irinta acikin kishiyoyi sai antona. Hajiya Bunayya kuwa nashiga kichen ta fashe da dariya mai ɗan sauti tace. “Shegiyar mata zaki ci Ubanki atunaninki har ƙasan raina nake sonki”. Sai kuma ta sake tun tsirewa da wata dariya mai sauti can ƙasa, kana ta ɗauki cup ta zuba mata Tea kana ta ɗauki Plate da spoon ta fita. Miƙa wa Mommy plate ɗin tayi tare sa faɗin. “Naga kamar kwana biyu bakyajin daɗi”. Ya mutse fuska Mommy tayi kana tace. “Wallahi kuwa gaba ɗaya bana jin daɗin jikina wannan karon kuma da laulayi sosai yazo min”. Cike da tausayawa Hajiya Bunayya tace. “Ayyah sannu Ubangiji Allah ya inganta”. Aranta kuwa cewa tayi Allah ya tarwatsa matsiyaciya. Ita ko Mommy tace. “Ameen ya Allah”. Miƙewa Hajiya Bunayya tayi tare da ɗaukan Plate din ta ɓude perpesoup ɗin dake tururi yana tashin ƙamshi ta zubawa Mommy tare da miƙa mata da kofin shayin. Lumshe idanu tayi sosai ƙamshin ya bugeta, a take yawunta ya tsinke abinka da mai cike lokaci ɗaya taji ranta yabiya da Perpesoup ɗin hannu tasa ta amsa tare da ajiye plate ɗin bisa cinyarta kana tasa spoon ɗin da sauri ta ɗebo sokar hanta da rokon ta perpesoup ɗin takai bakinta.....! *GARKUWAR* taku ce dai MA'AURATA, da masu shirin aure, da masu jego, da yan gayu masu son k’amshi kece raini, da gyaran da zaike maimaita muku dararen forkon kuruciya* Ko kunsan Jikinmu na da sinadaran hormones da suke taimakawa dan’adam akan komai musamman lokacin da mace take mu’amalar aure da mijinta. Mafi akasari wannan hormones din ne ke samun matsala ko su yi sanyi koma su daina aiki kwata-kwata shi ne dalilin da zai sa mace tace bata jin sha’awa ko bata san dadin aure ba. Albishirinku ina da kayan da ke taimakawa wannan sinadaran du dawo aiki tukuru don karkato miki da kimarki wajan mai gida sannan su taimakawa wannan sinadaran hormones dinki su dinka secreting din ni’ima wadatacciya da zata taimaka miki ki gamsu mijinki ya gamsu fiye da tunaninki. Note: Kayana ba sa tsinka ruwan ni’ima suna dai taimakawa hormones dinki ne su tsattsafo da ni’imar musamman wacca cutar sanyi ko dattin mahaifa ya dankarar da su ya hana su yin aikinsu yanda ya kamata. Haka zalika idan kina da kyau ki kara da wanka. Zaki iya amfani da magani na na gargajiya wanda zai gyara miki sex hormones din kullum ki kasance cikin humidify wato cikin damshi mai albarka kamar yanda ake son mace. Yana gyara miki mara. Sai kamshi. Hajiyata daure ki fara amfani da turarena ki ji irin salon kamshin sa salo ne da zai daidaita ki da mijinki ya kankaro miki da kimarki a wajansa. Siyan na gari mayar da kudi gida. Ga masu buƙata ga number' wayata wanda nake whatsApp dashi 09097853276 kimin mgn ta whatsApp in har kin tabbatar kin shirya saya mu dai-dai ta, kayana ba ƙanana bane, shiyasa bana harkan karanta, muddin kinsan baki shirya sayaba Please kada kiyi min mgn ki bari sai kin shirya kuɗinki a hannu, ba ina nufin kayana bana talaka bane, no akwai ƙananan set na masu karamin karfi, banson aimin mgn a ɓatamin lokacin aiyukana a shirme baki shiryaba. Shine karantan da bana so. 0005388578 Jaiz bank AISHA GARKUWA ALIYU. In kin shirya ga number ta ga kuma account number ta wanda in mun gama mgn zaki turo kudin ki, kana insa miki kaya a mota, duk ƙasar da kike kayana zaije gareki, amman fa in kinada dalilin zuwan nasune🤝🏻sayan na gari meda kudi gida. GARKUWAR MA'AURATA _By_ *GARKUWAN MARUBUTA* [19/07, 7:44 PM] Halimatu A/rahman Sadeeya: 📝✨💫⏰🤴🏻👹❤️❤️❤️🍇 *SAKAYYAH* _Page 11_ _NA_ *AYSHA ALIYU GARKUWA* 🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 *FREE PAGE fa ya kusa ƙarewa* *Littafin SAKAYYAH na kuɗine wannan Free page ne ƴar uwa 1k ne kacal 0661110170 GTBank AISHA ALIYU GARKUWA sai ki turo min shaidar biyanki ta WHATSAPP 09097853276. Sai in saki a Group ɗin.* *WOHOHO IN KAJI ANA ƘI GUDU TABBAS SA GUDU NE BEZO BA* _Ina kuke Ma'aurata masu sha'awar ganin sun zama taurari kuma fitilu a idanun mazajensu Uwar gida,Amarya,Tsakar gida,hadda tan kaɗen gida Shararriya kuma ƙasaitacciya data saba kawo muku nau'ikan sirrin sahihan magungunan ma'aurata wato *AYSHA ALIYU GARKUWA* Garkuwar Marubuta ayau ma ta dawo muku da Ingantattun magungunan mata masu kyau da inganci domin gyara kanki ki zamto tauraruwa a idanun mijinki...Muna da Ingantattun Abubuwa kamar haka_ :_Munada Garin mallaka, garin maɗi, garin Hakkin mayi, garin ɓelɗamhi Garin ilanwaddihi, Gumbar da ba'a baiwa mai kishiya, Gumbar kolli mai kellin al'khairi, Gumbar Riɗi wato 3 in 1, Gumbar makwaranyi, Masin Maliƙi mai masifar ƙarfi da matse mace, ka masin Daɗi har Maɗigan Akwai, kwanon ƙasaitacciyar mace mai masifar kyau da ratsa jiki da samar da inƙantacciyar ni'ima yanada abubuwa masu kyau haɗinsa, Zumar goron tula mai masifar kyau, tsumin dabino, mai ratsa jiki, tsumin Riɗi mai ƙarfi, Furar Mata mai tsastsafo da ni'imantaccen damshi, Cida kaza, Ciccibi Abodi, Tsumin Ɓaure, tuwon ɓauren, kana akwai maganin sanyi sadidan, da dai sauransu...Se kuma fannin ƙamshi kasance da Shu'umin ƙamshi wanda ze gigita ƙwaƙwalwar Oga tare da jin ko wacce mace bata kaiba...._ _Shin ko kina da labarin Miskilinci da ƙasaitar Rayyan Naaan amma lokaci ɗaya ya zamto zautacce sakali akan soyayyar Jannart bakomai Jannart ta riƙe ba face sirrinkan gyara da kuma shu'uman humran da kulaccar sirri na Aysha Aliyu Garkuwa(Tubali) tabbas taga tasirin haka domin Naanunta ya zame mata tamkar bawa_ _Shin ko kinsan sihirtaccen haɗin da Aysha ke sha kenan ta zamto tauraruwa a idanun Hamma Yusuf(Miwasmiti)...Tabbas Mahmud ya zamto zautacce kuma makaho akan sauyayyar Bazawara wato khadijarsa duk da kuwa gashi da budurwa(Namiji Baya Kaɗan) ko kinsan hakan nada alaƙa da amfani da sahihan maganin da kuma shu'uman humran Aysha Aliyu Garkuwa??.Nasan ba zaka ku manta da irin kima da kuma darajar da Aysha ke dashi acikin Idanun Sheik Jabeer ɗin ta duk da kuwa shekaru sunja anma jinta yake tamkar budurwa 'yar sha bakwai(Garkuwa) sirrin hakan na tare da Ingantattun kuma sahihan magungunan Aysha Aliyu Garkuwa Wato Garkuwar Marubuta da kuma Ma'aurata na tabbata kunsan da cewa basirarta ba'a iya rubutun littafi ya tsaya ba hadda inganta rayuwar ma'aurata ta hanyar kawo musu Nagartattun abubuwa Ga duk wacce ta shirya saya seta tuntuɓi number ta 09097853276 muna iya tura kayan mu aduk inda kuke afaɗin Nigeria harma da ƙetare Dan Allah 'yar uwa idan baki shirya siyaba kada kiyi min magana muɓatawa kanmu lokaci...._ 🤝🏻🤝🏻🤝🏻🤝🏻🥰😘sai.kunzo. sayan na gari maida kuɗi gida, Cikin lumshe Ido Mommy ke cin perpesoup ɗin yayin da daɗinsa ke ratsa ilahirin jikinta, kallonta Hajiya Bunayya dake murmushi tayi tare da ɗiban romon da cokali takai bakinta kana ta buɗe Idanunta dake lumshe. Tace. “Gaskiya Yaya Nagode wallahi bakiji yanda naji daɗin Perpesoup ɗin nan ba, dama sai tunanin a binda zanci nake tuntuni sai kuma gashi Allah ya kawo ki”. Murmushi mai cike da Ma'anoni Hajiya Bunayya tayi kana ta muskuta tare da gyara zamanta tace. “Lallai de kam aidama sanyin nan saida abu mai ɗumi da ɗan yaji-yaji”. Yayin da aƙasan ranta wani irin farin cikine mara misaltuwa wanda har yakasa ɓoyuwa asaman fuskanta. Ita kuwa Mommy Sosai take cin perpesoup ɗin tana mai lumshe Idanunta yayin da daɗin sa ke ratsa har ƙwaƙwalwar kanta tace. “Yaya perpesoup ɗin nan yaji kayan yaji”. Dariya Hajiya Bunayya tayi tace. “Dama Alhaji nayiwa nace bari na zubo miki dan nasan zaki ji daɗin sa”. Kai Mommy ta gyaɗa da faɗin. “Aikam gashi yamin daɗi sosai”. Acan ɗaki kuwa miƙewa tsaye Khausar tayi daga kan stool tare da riƙe ƙugunta ta bayan ta gama nin ke kayan asaman laɓɓannta ta furta. “Wash Allah!, Gashi yanzu na gama gyara kayan nan, amma Raudat na zuwa ɗaukan abu ɗaya zata wargaza shi kab, ya zama kamar ba'a taɓa gyarashi, amma Insha Allah next time, Idan ta ƙara har gitsashi, sama Zan mayar dan kayanta, ta yanda idan tazo baza ta iya ɗauka ba sai ta kirani in bata yafiye min sauƙi”. Ta Ida maganar tare da fitowa falon tana riƙe da ƙugunta da hannu ɗaya yayin da ɗaya hannun ke dafe asaman wuyanta. Cike da mamaki take kallon Hajiya Bunayya dake zaune yayin da Mommy ta ke shan perpesoup ɗin da kaɗan ya rage asaman Plate ɗin. Cikin yanayin tashin hankali da razana Khausar ta ɗaga Muryanta tace. “Mommy me kike ci?". Anitse Mommy ta ɗago kanta dan sam batasan ta fito ba sai da taji muryanta, gyara rikon Plate din Mommy tayi kafin tace. “Perpersoup ne ko zaki cine?”. Ita kuwa Khausar kai ta girgiza cikin rawan murya tace. “A'a nikam bazan ciba Mommy kekam Komai kika samu sai kinci, ba zaki tsaya ki duba ingancin sa da kuma rashin ingancin saba”. Baki Mommy ta sake tana kallon Khausar da Mamaki. Ita kuwa Hajiya Bunayya wani mugun Harara ta galla mata cike da tsanarta tace. “Komai ta samu saita ci ke kin isa ki hanata cine?, Khausar!, Khausar!!, Khausar!!! ki kiyayeni fa”. Ta Ida maganar tana dariya irin abin awasa takeyin sa, yayin da kuwa azuciyarta ba haka bane. Ita kuwa Mommy taɓe Baki tayi tace. “Yaya rabu da ita itama kanta kwaɗayin ya kawota ƙilan so take in bata”. Fuska Khausar ta ɓata cike da damuwa tace. “Wallahi nikam ba zanci ba Mommy kema Meyesa zakici, kema daga ganin abu saiki hau ci, batare da kin duba ingancin sa ba Allah ma dai yasa kinyi Bismillah”. Dafe kai Mommy tayi tace. “Aikuwa de Wallahi kwaɗayin sa yasa na shafa banyi Bismillah ba, Anma bari nayi. Bismillahi feh Auwalihi Wa'ahirihi”. Ta faɗa tare da cigaba da shan perpesoup ɗin. Wani banzan kallo me cike da tsana Hajiya Bunayya ta watsa wa Khausar aranta tace, shegiyar yarinya, wannan yarinyar saina bi takan ta tukunna zata gane kurenta, bari dai ingama da matsalolin dake gabana”. Ita kuwa Khausar kallon mahaifiyarta da har zuwa yanzu take shan perpesoup ɗin tayi tace. “Wai Mommy ba zaki haƙura dasha haka ba?". Girgiza Kai Mommy tayi kana tace. “Kema Idan zaki ci ga shican akula Khausar ban hana kiba, amma wannan tambayoyin naki sun fara isata”. Ƙwafa Hajiya Bunayya tayi tace. “Ƙyaleta bare ma ni bazan bar mata ba ina kedai ya isheki?”. Cikin sakin fuska Mommy ta gyaɗa kai tare da faɗin. “Eh Alhamdulillah ya isheni”. “Aiko buƙatar maje haji salla, ba zan bar matashi ba, tunda dai ke kinsha ai hikenan, idan tanaso ta biyoni ɗakina”. Ta ida maganar tare da ɗaukan kularta ta fice bayan ta yiwa Mommy sai anjima. Zama Khausar tayi agaban mahaifiyarta cikin raunin murya da yanayin damuwa tace. “Mommy meyesa!?, Rayuwar nan fa ba yanda kika ɗauke ta da yanda zuciyarki take ace haka na kowa yake da munji daɗin duniyar nan fa, amma Mommy meyesa daga kawo miki abu zaki ɗauka kici yanzu kuma idan abin cutarwa ne fa?”. Kallonta Mommy tayi cikin tsukr fuska kana cikin fushi tace. “Khausar ki kiyayeni fa, bana son wannan baƙin halin da kike ɗaurawa rayuwarki fa. Ni bakiga ina nunawa matar nan baƙin hali ba haka zalika itama da zuciya ɗaya take zaune damu, zaman lafiya mukeyi babu kishi bare tsangoma ko hassada, amma meyesa zaki sawa ranki rashin yarda akan n Me kike zaton zata cutar dani, babu abinda zata yimin dan haka ki kiyaye”. Ita kuwa khausar hawaye da ya cika mata Idanunta tashiga ƙoƙarin mayarwa sabida takaici, mahaifiyarta ta ɗauki duk kan yarda da amana ta basu, amma sukuma da wannan damar suke amfani ganin sun cutar da rayuwarta. Ƙasa Tayi da kanta kana tace. “Shikenan Mommy Komai na faɗa miki ba zaki yarda dani ba, amma babu komai Ubangiji Allah yatsareki ya kuma kareki". “Ameen”Mommy ta amsa a kufule. Ita kuwa Khausar cikin mutuwar jiki ta miƙe tare da wucewa Bedroom ɗinta tana maijin wani irin zafi azuciyarta. Da kallo Mommy tabi bayanta tana ayyana abubuwa da yawa akanta, tarasa ina Khausar ta ɗauko wannan halin baki ɗaya bata da yarda muddin Hajiya Bunayya zata kawo mata abu ko Haiydar saita tsaya tana musu tambayoyi akai, da faɗin kada suci kada suyi kaza da kaza. Jin ƙiran sallah magriba yasa ta miƙe tashiga Bedroom ɗin ta dan gabatar da Sallah. Aɓangaren Khausar kuwa tana shiga ɗaki ta lumshe Idanunta tare da manna bayanta da jikin ƙofa. Hawaye masu ɗumi suka zubo mata jikinta na bata da wani makircin da Hajiya Bunayya ta shiryawa mahaifiyarta sam bata yarda da wannan perpesoup ɗin da takowo mata ba, shin wai ma ta wani hanya zatabi ta fahimtar da mahaifiyar?. Sosai ta zurfafa acikin tunanin da take har aka shiga Masallaci sai, asannan ta sauƙe gauron numfashi tare da nufar toilet cikin nutsuwa ta ɗaura alwala kana ta fito, tare da shimfiɗa darduma duk da yanayin zullumi da take ciki bai hanata tattara nutsuwarta zuwa ga Ubangiji mabuwayi gagara Misali ba, bayan ta sallame ta ɗaga hannayenta biyu zuwa sama kana tace. “Ya Allah baka zalinci sannan kai ka hana zalunci atsakaninmu ya Allah baka gyan-gyaɗi bare bacci ya Allah kada ka bawa wannan baiwar taka daman cutar damu ya Allah ka kare mahaifiyata al'farma Annabi da al'ƙur'ani”. Kana ta shafa addu'ar tana mai zubar da hawaye har aka idar da Isha'i bata fita ba saima miƙewa da tayi ta kwanta agado lamo cike da tunanin rayuwa da haka bacci mara daɗi ya ɗauke ta. Cikin ikon Allah haka Mommy ta kwana lafiya lau batare da wani mugun abu ba, tun Khausar na jira taji Mommy tace wani wajen nayi mata ciwo ko kuma taga zubewan cikin Mommy kamar yanda Hajiya Bunayya ta faɗa taji shiru, hakan yasa ta watsar da abin aranta yayin da Aɓangaren Hajiya Bunayya baki ɗaya kunnenta ke sauraron jin wani labari daga bakin Mommy sai dai shiru amma tace bari ta kara jira kaɗan ta gani. Yau kwanan Mommy uku da cin perpesoup ɗin da Hajiya Bunayya ta kawo mata tana zaune a Bedroom ɗin ta cike da kasala. Cikin rumtse idonta ta zabura tare da dafe ƙasan maranta da yayi wani masifan murɗawa ahankali ta furta. “Wash! Allah na”. Sai kuma ta koma ta zauna tare da lumshe Idanunta yayin da hannunta na dama ke dafe asaman maranta sai ka ta miƙe tare da fitowa falon tana takawa ahankali. Khausar dake zaune a asaman 3sitter Jikinta sanye da half gownt na bacci yayin da ta tura tulin sumar kanta acikin hular Net Idanunta na kan takardan Geography dake riƙe ahannunta yayin da Nahawu ke ajiye gefe ta ɗago manyan Idanunta ta zubasu akan Mommy dake ya mutse fuska alamar bata jin daɗin jikinta, zama tayi akan 1 sitter kana a hankali tace. “Khausar har yanzu baki shiga ba?”. ta ida mgnar tana mai cije lips ɗinta. Ita kuwa Khausar kai ta gyaɗa mata tace. “Eh Mommy karatu nakeyi, gobe Idan Allah ya kaimu zamu fara Exam ɗin First term, lokacin ai ya tafi amma Mommy lafiya na ganki haka?”. Ta ƙare mgnar tana kafe mata ido. Ya mutse fuska Mommy tayi tare da lumshe Idanunta still cikin na damƙarta tace. “Wallahi cikina ke ɗan min ciwo Khausar”. Cike da tausayawa Khausar tace. “Cikin ki kuma Mommy?”. Kai Mommy ta gyaɗa tace”. “Eh”. Ita kuwa Khausar ajiye takardan hannunta tayi tare da tsirawa mahaifiyarta ta Ido cikin tausayawa tace. “Mommy kodai in faɗawa Abba Azo atafi Asibiti ne?". Kai Mommy ta girgiza kana tace. “A'a ai beyi tsanani har haka ba”. Kai Khausar ta gyaɗa tare da sauƙe numfashi tace. “Toh Allah ya sawwaƙe”. Mommy da hannunta ke dafe asaman cikinta still Idanunta na lumshe tace. “Ameen” Miƙewa Mommy tayi ta koma kan 3sitter ta kwanta kamar minti biyu da kwanciyarta ta sai kuma sake miƙewa ta zauna tana yamutse fuska. Ita kuwa khausar cikin yanayin damuwa tace. “Sannu Mommy kode in Kira Abba ne?”. Girgiza kai Mommy ta kumayi sannan tace. “A'a tashi ki koma ɗaki nima yanzu zan shiga na kwanta”. Girgiza kai Khausar tayi tace. “A'a Mommy Zan zauna dake”. Lumshe idanu tayi tare da cije laɓɓanta na ƙasa tace. “Kada ki damu kije ki kwanta na faɗa miki naji sauƙi kuma nima yanzu zan shiga na kwanta”. Cikin sanyin jiki ta mike kana tace. “Saida safe Allah yaƙara sauki”. Mommy ta amsa da “Ameen”. Ita kuwa Khausar tana shiga ɗaki ta zube akan gadonta tare da faɗa wa duniyar tunanu, a haka bacci ya ɗauke ta kasancewar dare yaja batayi bacci ba ga kuma gajiya. A ɓangaren Mommy kuwa haka ta kwana cikin mawuyacin hali tare da murƙusoso cikin matsanancin ciwon ciki. Washe gari. Da safe bayan Khausar na idar da Sallah tayi Azkhar ta nufi ɗakin Mommy bakinta ɗauke da sallama. Mommy dake kishingiɗe kan darduma ta ɗago kanta tare da amsa sallamar Khausar. Kusa da ita Khausar ta tsugunna tare da riƙe hannunta tace. “Mommy ina kwana ya cikin naki?”. “Murmushin Ƙarfin hali Mommy tayi kana tace. “Naji sauƙi Khausar kije ki haɗa muku abin Breakfast kada lokaci ya ƙure”. Kai Khausar ta gyaɗa kana tace. “Amma da sauki Mommy kodai daurewa kike yi?”. Murmushi Mommy tayi tace. “Eh jeki shirya muku”. Kai ta gyaɗa sannan ta fice kai tsaye kichen ta nufa. Tana shiga tasa ruwa kadan atukunya yanda zai wadatar mata bayan ya tafasa ta ɗan zuba mai kana ta zuba Couscous kamar minti goma ta buɗe taga ya dahu yayi sar gwanin kyau, amfanin ɗiga man kenan. Sauƙewa tayi sannan ta buɗe fridge ta ɗauko miyan stwe da yaji naman kaza ta ɗumama sai kuma ta dauko lunch box din Raudat, Ramadan da Haiydar da kuma nata ta zuba musu, sai kuma ta koma ɗaki tashiga toilet tayi wanka Agurguje ta fito ɗaure da towel mai ɗan girma sannan ta cirewa Raudat kayanta tayi mata wanka bayan sun fito tashafa mata mai kana ta sanya mata Uniform sannan itama ta shirya cikin Uniform da yayi matukar amsar jikinta hannu Raudat taja suka fita dai-dai lokacin da Haiydar suka fito da Ramadan cikin shiri ko wannensu ya nufi inda lunch box ɗin da yake ya ɗauka kana suka fice harabar gidan suka shiga mota. Kamar ko yaushe motar na parking Khausar ta fito riƙe da hannun Raudat, Sai da ta kaita ajinsu sannan cikin sauri ta juya ta kama hanyar koma ajinsu daga baya taji ankira sunan ta da faɗin. “Lelewal ke kullum sai kowa ya riga ki shiga cikin aji ko?”. Ahankali ta juya tare da sauƙe manyan Idanunta akan Malam Isa dake tsayi murmushi tayi da faɗin. “Ba haka bane Malam na tsaya kai Raudat ajinsu ne shiyasa”. Kai ya gyaɗa still Idanunsa akanta hakanan yarinyar ke burgesa ahankali yace. “To ki tafi kar araba musu questions paper ba kyanan”. Kai ta gyaɗa tare da juyawa cikin sassarfa da sanin darajar kanta take tafiya har ta isa cikin ajin. Aɓangaren Amina kuwa koda M Jameel yashiga class da niyyar raba musu questions paper ƙasa tayi da kanta ta amsa batare data kalli fuskarsa ba domin koda gaishesa ne ta dena tunda ta lura da baya buƙata kallon fuskanta, to shima M Jameel Sosai yaji daɗi da yarinyar ta daina gaishesa, dan ko kaɗan baya ƙaunar kallon fuskarta, bare kuma wata magana ta haɗa su. Acan gida kuwa tun bayan tafiyar su Khausar Makaranta cikin Mommy ya tsananta da ciwo da ƙyar ta yunƙura ta miƙe tana mai rintse Idanunta jini taga yana bin ƙafafunta da sauri ta dafe cikinta da ƙyar ta iya furta. “Ya Allah wannan ciwon cikin kuma na menene?”. Da ƙyar taja ƙafanta zuwa jikin beside drawer ta ɗaga wayarta tare da kiran number Hajiya Bunayya, kafin ya katse Hajiya Bunayya tayi picking tare da Sallama. Mommy kuwa cikin azaban ciwon da cikinta ke mata ta rintse Idanunta kana tace. “Yaya”. Da sauri Hajiya Bunayya ta katseta da faɗin. “Ƙanwata lafiya naji muryanki haka?”. cike da yarda ta rintse Idanunta cikin yanayin azaban ciwon da cikinta keyi tace. “Wallahi Yaya cikina ciwo yake tun daren jiya, haka na kwana banyi bacci ba yanzu kuma gashi jini ya ɓalle min! Dan Allah ki faɗawa Alhj mutafi asibiti”. Hajiya Bunayya kuwa da damuwa amuryanta tace. “Subhanallahi! bari na faɗa masa yanzu ma kuwa”. Sannan ta katse wayar ta nufi ɗakin Lamiɗo ranta fari Sol burinta ya cika abakin ƙofa suka haɗu yana shirin fita. A take ta wani marairaice fuska kana cikin yanayin damuwa tace. “Yanzu Mommyn Khausar ta kirani. Wai jiya da ciwon ciki ta kwana yanzu kuma jini ya ɓalle mata”. Ai bai ma gama sauraron abinda zata faɗa ba ya ratsa ta ya wuce sashen Mommy cike da damuwa. Hajiya Bunayya kuwa da harara tabi bayansa kafin taja siririn tsaki ta mara masa baya. Tana shiga Bedroom ɗin ta samu Lamiɗo tsugunne akan Mommy da sauri ta tsugunna daga gefensa ta riƙo hannun Mommy. Cike da tausayawa kamar za tayi kuka tace. “Sannu Aysha ciwon ciki amma baki yi magana ba, gashi har ya tsananta jini na zuba”. Ta ida maganar zufa na karyo mata wanda in kagani zakayi zaton na tsananin damuwa ce, nan kuwa na tsananin farin cikin burinta ya cika ne. Lamiɗo kuwa miƙewa yayi tare da naɗe hannun rigarsa zai ɗauke ta Ganin haka ne yasa Hajiya Bunayya tayi saurin miƙewa tare da tallafo Mommy jikinta suka fita, agidan baya suka zauna Lamiɗo kuma ya shiga gefen mai zaman banza Driver yaja suka tafi Hajiya Bunayya sai faman sannu take yiwa Mommy. Suna isa asibitin aka karɓe su kai tsaye emergency aka nufa da ita ganin cikin ya riga ya zube yasa likitoci suka nufi wani ɗaki da ita tare da yi mata wankin ciki kana suka yi mata allurai nanda nan bacci wahala ya ɗauke ta Lamiɗo kuwa kasa Matsawa daga kusa da ita yayi ya cike da kulawa ya zauna a bakin gadon tare da riƙe tafin hannunta cike da tausayinta. Hajiya Bunayya data shaƙa ta cika kuwa. Wani lalataccen harara ta watsawa ƙeyansa cikin ranta tace, tabbas sai tayi wani abu akan wannan rawan jikin da yake mata. A zahiri kuwa dafa kafaɗar sa tayi, ahankali ya ɗago kansa ya kalleta da idanunsa dake cike da damuwa amma baice komai ba. Cike da kirsa ta ƙirƙiri murmushin da bai kai zuciba kana tace. “Dan Allah ka rage damuwar nan, babu yanda zamuyi da ƙaddara haka Ubangiji ya tsara wannan ɗin ma ba rabo bane, ayanzu addu'ar lafiya take da buƙata awajenmu”. A hankali ya sauƙe nannuyar Ajiyar zuciya tare da mayar da Kallonsa ga Mommy dake bacci tamkar babu abinda ke damunta. Lumshe idanunsa yayi yace. “Ina matuƙar tausayawa Aysha tun bayan haihuwar Haiydar take fama da wannan matsalar sannan ko wanne cikin sai ya wahalar da ita kafin ya fita”. Da sauri Hajiya Bunayya ta katsesa da faɗin. “Ya zamuyi da rubutacciyar ƙaddara, ai kaga da Ubangiji yaga dama ai cikin Raudat da Ramadan ya zauna”. Kai ya jinjina amma baice komai ba. Ita kuwa cikin ɓoye farin cikinta ta sauƙe ajiyar zuciya da faɗin. “Zan koma gida kafin ‘yan makaranta su dawo, naga lokaci yaja amma Insha Allah anjima zan dawo”. Kai ya gyaɗa ba tare da yace komai ba still Idanunsa na kan Mommy. Hajiya Bunayya kuwa ficewa tayi ranta fari fess kana tasa Driver ya maida ta. Acan Makarantar su Khausar kuwa koda suka gama Exam ba abasu damar tafiya ba bayan sunyi sallar la'asar suka shiga haddar Alkur'ani sai ƙarfe biyar aka tashe su, kana suka shigo mota suka nufi gida, motar na parking Raudat ta fice da gudu ta nufi sashen su Tana shiga falo ta fara kiran. “Mommy! Mommy!! na mun dawo”. Jin shiru yasa ta nufi Bedroom ɗinta da gudu ta buɗe ta shiga tana kiran. “Mommy!, Mommy!!, Ina kika shiga”. Still Bata ganta ba da gudu ta juya ta fito falon dai-dai lokacin Khausar kuma ta shigo ƙara sawa kusa da Khausar tayi ta riƙe hannunta kana tace. “Addah Khausy Ina Mommy?”. Kallonta Khausar tayi kafin tace. “Bata ɗaki ne?”. Kai Raudat ta gyaɗa mata alamar Eh, Sake hannunta Khausar tayi kana ta nufi kichen ta buɗe wayam tagani alamar bata nan komawa tayi ta shiga Bedroom din ta ɓude still ba tanan jikin toilet ta nufa ta manna kunnenta ajiki tare da faɗin. “Mommy Mommy kina ciki kuwa?”. Jin shiru yasa ta tura ƙofar toilet din still bata nan fitowa tsakiyar falon Khausar tayi tare dasa hannun damanta ta riƙe ƙugunta tana tunanin ina Mommy ta shiga haka, bayan tasan bata fiye fitar yamma ba kuma koda zata fita tun safe kafin su tafi makaranta zata faɗa musu bare kuma yau da suka barta bata jin daɗi. Da sauri ta kalli Raudat sai kuma tace. “Jirani anan ina zuwa”. ta faɗa tare da ficewa kai tsaye sashen Hajiya Bunayya ta nufa bakinta ɗauke da sallama tana faɗin. “Ummah”. Shigar ta yayi dai-dai da lokacin da Hajiya Bunayya ke riƙe da waya tana cewa. “Kedai Hajiya Lami bari buƙata ɗaya ta biya saura ɗaya, tana can kwance a asibiti cikin ya zube yabi makwarari, saura ɗayan daman jira nake inga ya zata kaya ne ki shirya jibi zamu koma”. Komai Hajiya Lami ta faɗa ohon musu, ita dai Hajiya Bunayya cikin jin dadi ta kece da wata mahaukaciyar dariya mai nuni da tsantsar farin ciki. Lokaci ɗaya kuma dariyar nata ya tsaya ganin Khausar tsaye, sai kuma ta katse kiran tare da kallon Khausar. Kafin tace wani abu Khausar tayi saurin cewa. “Ummah ina Mommy mu?”. Hajiya Bunayya ta wani langwaɓar da kai kana tace. “Ayyah Khausar am Mommy ku tana asibiti bata da lafiya wallahi cikinta ya zube”. Da sauri Khausar da kanta ke ƙasa ta ɗago ta kalli Hajiya Bunayya tana sake maimaita kalmar cikinta ya zube akasan ranta lokacin ɗaya hawaye masu zafin gaske suka cika kwarmin Idanunta. Sai kuma tayi saurin maida hawayen ta kafin tace. “Shikenan ɓuƙatar magauta tabiya hankali ya kwanta. Allah ya raya mata wa anda ta haifa. Ubangiji ya tsaresu daga sharrin mai sharrin”. Ta ida maganar tana ƙoƙarin fita. Da sauri Hajiya Bunayya tace. “Ke Khausar zo nan Me kike nufi?”. Anutse Khausar ta juya tare da sauƙe manyan Idanunta da suka sauya launi zuwa ja ta zubawa Hajiya Bunayya kana tace. “A'a Ummah babu abinda nake nufi, kawai dai addu'a ce nayi”. Cikin tsuke fuska Hajiya Bunayya ta watsa mata Harara da faɗin. “Sannan su waye ne Magautan?”. Ware hannu Khausar tayi tare da faɗin. “Nikam ban sansu ba, amma dai nasan Allah Mabuwayi gagara Misali ya sansu kuma zaiyi maganin su, domin ai bahaushe yace rana dubu ta ɓarawo rana ɗaya ta mai kaya, suji tsoron ranan da Ubangiji zai musu kamun talala!”. Cike da Mamaki Hajiya Bunayya tace. “Wai Khausar me kike magana kamar habaici kike min ko kuma hannunka mai sanda!?.” Ware ido Khausar tayi tace. “Haba Ummah in Miki habaici kuma ayanda kike ƙaunar Mommyn mu kinfi ƙarfin habaici ko hannunka mai sanda kin wuce haka sai dai mgnar ce tazo kamar zaurance”. Ɓoyeyyen Ajiyar zuciya Hajiya Bunayya ta saki domin tayi zaton yarinyar ta gano lagonta ne. Khausar kuwa murmushi tayi tare da faɗin. “Bari na tafi asibitin kar dare yayi”. Da sauri Hajiya Bunayya ta gyara zamanta Idanunta akan Khausar tace. “Toh kibari in ƙara sa abinci mana sai ki tafi dashi”. Kai Khausar ta gyaɗa da faɗin. “Toh amma bari na shiga gidan Aunty Ruƙayya kafin ki ƙarasa”. Kai Hajia Bunayya ta gyaɗa tare da faɗin. “Toh ki gaisheta”. Kai kawai Khausar ta gyaɗa Sannan ta wuce sashen su. Tana shiga Bedroom direct toilet ta wuce ta cire Uniform ɗin ta sannan ta watsa ruwa bayan ta fito ta dauki dogon rigar material pinch colour ta sanya, kana ta nufi kichen Agurguje ta dafawa su Haiydar jollof ɗin shin kafa da yaji bushesh-shen kifi da kayan ƙamshi nan da nan kichen ɗin ya ɗauki ƙamshi Warmers ta ɗauka ta juye sannan ta tafasa musu tea kana ta ɗura musushi, sannan ta fita falon dai-dai lokacin da Haiydar ya shigo. Kallonsa Khausar tayi tare da kiran sunansa tace. “Haiydar”. Ya amsa da. “Na'am”. Cikin sanyi tayi ƙasa da muryanta tare da faɗin. “Dan Allah Haiydar ka kwana anan kai da Ramadan, Raudat kuma zamu tafi da ita asibiti sai mu kwana da Mommy”. Kai ya gyaɗa mata sai kuma yace. “Nima ai inaso naje na dubata”. Jinjina kai Khausar tayi tace. “Ba damuwa kazo mutafi dukan mu amma yanzu zan fara shiga gidan Aunty Ruƙayya in sanar mata, idan yaso kai da Ramadan ku taho tare da Ummah, In yaso sai ku dawo tare amma kubar min Raudat dan zamu kwana tare”. “Toh shikenan Allah ya bata lafiya”. “Ameen”, Tace kana ta juya ta tafi har ta kusa fita ta sake juyawa ta kalli Haiydar dake tsaye Ahankali tace. “Dan Allah Haiydar ka kula, bakomai za'a baka kaci ba, akwai abinci na dafa muku sannan duk wani abu da zaku buƙata akwai”. Da sauri ya dafe kansa tare da faɗin. “Ke dai jeki da rashin yardan ki kedai haka Allah ya halicce ki baki da yarda”. Cikin sanyi ta girgiza kai kana tace. “Shikenan ni dai ban san sai yaushe zaku yarda dani ba”. Ta ida maganar tare da ficewa”. Kai tsaye gidan Aunty Ruƙayya ta nufa. Tare da Sallama tashiga Babban falon da yaji kayan alfarma kujerun set biyu aciki Black and Ash sai kuma babban tv plasma dake Manne abango daga ƙasansa kuma horm teater ne ƙasan falon kuma shimfiɗe yake da chanis capet. Aunty Ruƙayya dake bedroom ta fito fuskarta ɗauke da murmushi tace. “Khausar kece sannu da zuwa, shigo ciki”. Da sauri tace. “A'a Aunty sauri nakeyi ai”. Cikin kulawa tace. “Yo yasu Mommy ki?”. Murmushi Khausar tayi tace. “Wallahi Aunty Ruƙayya Mommy ce ke asibiti bata da lafiya, shine nace bari nazo na faɗa miki, Ni yanzu ma zan wuce ko za muje tare?”. Cike da tausayawa Aunty Ruƙayya tace. “Ayyah Allah ya bata lafiya zanje bari ina zuwa mu tafi tare”. Kai Khausar ta gyaɗa da faɗin. “Toh”. Aunty Ruƙayya kuwa bedroom ta shiga tare kiran mijinta a waya, bayan ya bata izinine, ta ɗauko key mota da mayafinta suka fita, suka shiga mota, jingina kai Khausar tayi da jikin motar kalaman Hajiya Bunayya nayi mata suwwa akunne. Juyawa Aunty Ruƙayya tayi ganin yanda Khausar ta zurfafa cikin tunani yasa tace. “Ki riƙa yi mata addu'a”. Kai kawai Khausar ta iya gyaɗa mata. Cikin Mintuna kaɗan suka isa Asibitin bakinsu ɗauke da Sallama suka shiga ɗakin da aka kwantar da Mommy saboda Hajiya Bunayya ta faɗa mata. Kwance akan gado suka tarar da ita yayin da Lamiɗo ke gefenta akan kujera hannunsa riƙe da kofin tea yana miƙa mata da faɗin. “Ki tashi kisha”. Yana jin Sallamar Khausar ya juya yana kallonta har ta isa kusa dashi. Cike da kulawa yace. “Khausar har kun dawo?”. Kai ta gyaɗa kana tace. “Eh Abba ya jikin Mommy!?”. Sai da ya ɗan kalli Mommy dake jingine da pillow sai kuma ya mayar da Kallonsa kan Khausar yace. “Da sauƙi”. Sai asannan ya lura da Hajiya Rukayya ya ɗan yi murmushi da faɗin. “Hajiya Ruƙayya sannu da zuwa”. Zama tayi akujeran dake kusa da ita tana cewa. “Yawwa ya Hajiya Aysha da jikin kuma?”. Ɗan Murmushi yayi kana yace. “Da sauƙi”. Tana kallon Mommy tace. “Ubangiji Allah ya ƙara sauki”. Ya amsa da. “Ameen ya hayyu ya ƙayyum”. Khausar kuwa bakin gadon ta ƙarasa ta riƙe hannun Mommy acikin nata. Cikin raunin murya tare da tausayawa mahaifiyar tata tace. “Sannu Mommy ya Jikin?”. Lumshe idanu Mommy tayi kana ta buɗe su a hankali tace. “Da sauƙi Khausar bana jin komai in dan ta nice ma, da su sallame ni in koma gida mu kwana tare, dan bana jin ciwon cikin yayi sauƙi babu inda yake min ciwo!”. Ajiyar zuciya Khausar ta sauƙe tare da faɗin. “Masha Allah Mommy Allah yaƙara sauƙi Ubangiji ya ƙara tsarewa ya kare”. A ranta kuwa cewa tace. Ayyah da ace duk addu'o'in da takeyiwa Mommynta tun randa taci ferfesun da ace tana haɗa addu'ar da yaron cikin wata ƙil da bai zube ba. Shafa kanta Mommy tayi cike da ƙaunar ta tace. “Ameen Khausar ki kwantar da hankalin ki ba najin Komai”. Ta faɗi hakan ganin yanda Khausar tayi zuru-zuru da ita. Hajiya Ruƙayyance ta kalli Mommy kana tace. “Hajiya Aysha ya ƙarfin jikin!?” Murmushi Mommy tayi kana tace. “Dasauƙi Hajiya Ruƙayya ya ‘Yar taki ya kuma rigima a makaranta!?". Kallon Khausar Hajiya Ruƙayya tayi kana tace. “A'a yanzu ai ta daina ta fara girma!”. Jin haka yasa Khausar tayi murmushi. Lamiɗo kuwa miƙewa yayi idanunsa akan Mommy yace. “Toh shikenan bari na tafi dama ganin babu kowa ne yasa nake zaune bari na samu naje nayi wanka dan tunda muka zo ban samu na koma gida ba”. Hajiya Ruƙayya tace. “Ayyah ai babu komai Alhaji kaje”. Jinjina kai Mommy tayi tace. “Allah ya tsare”. Ya Amsa da. “Ameen”sannan ya juya ya fice. Tafiyar Lamiɗo babu daɗewa Hajiya Bunayya da Hajiya Lami suka zo Raudat na riƙe da hannunta. Suna shiga Hajiya Bunayya ta zauna daga gefen gadon tare da kallon Mommy tace. “Sannu ƙanwata ya ƙarfin jikin?”. Murmushi Mommy tayi kana tace. “Ai naji sauki Yaya”. Jinjina kai Hajiya Bunayya tayi cikin yanayin tausayawa tace. “Allah ya baki lafiya”. Hajiya Ruƙayya kuwa kallo ɗaya tayi wa Hajiya Bunayya da Hajiya Lami taji sam basu kwanta mata arai ba musanman ma Hajiya Bunayya dake wani shish-shugewa Mommy. Ta dai daure tace. “Sannunku da zuwa”. Hajiya Bunayya da Hajiya Lami suka haɗa baki wajen cewa. “Yawwa ya mai jikin”. Ataƙaice Hajiya Ruƙayya tace. “Da sauƙi”. Hajiya Lami kuwa jikin gadon ta matasa Idanunta akan Mommy tace. “Ayyah Sannu Hajiya Aysha Ashe ga abinda ya faru kuma? Amma wannan abu yayi yawa ai gwara Alhj yayi ƙoƙari ya fitar dake waje wannan matsalar ko yaushe da ansamu ciki ya zube ai babu daɗi!”. Kafin Mommy tayi magana Hajiya Bunayya tayi saurin cewa. “Kede bari Hajiya Lami abin nan yana damun mu, gaba ɗaya mun kasa gane menene ainihin matsalar, amma hankalinmu na tashi kullum cikin yanayin nan, abin babu daɗi yanzu ciki takwas kenan yana zubewa abin ai babu daɗi!”. Taɓe baki Khausar da Hajiya Rukayya sukayi alokaci ɗaya. Ahankali Mommy ta gyara matashin data kishingiɗa akai kana tace. “Uyummm ya za'ayi da abinda Allah ya tsara, amma ni inaga nin ba wani matsala bane, tun da gashi na haihu bayan haihuwar Haiydar ma haka nata fama da ɓare-ɓaren nan, kuma daga baya da Allah ya kawo Ramadan da Raudat an haifesu ba komai ai”. Cike da kirsa Hajiya Bunayya tayi yaƙe kana tace. “Hakane kam, toh Allah ya kawo masu albarka”. Hajiya Lami kuwa harara ta gallawa Mommy tare da taɓe baki aranta tace shegiya me iyayin jaraba keda haihuwa sai dai kiga anayi. Idanun Hajiya Ruƙayya da Khausar na kan Hajiya Lami alokacin data taɓe baki ta harari Mommy, Juyawa Hajiya Ruƙayya tayi ta kalli Khausar tare da jinjina kai itama Khausar kai ta jinjina. Miƙewa Hajiya Ruƙayya tayi tare da kallon Mommy tace. “Toh Hajiya Aysha Ubangiji Allah ya ƙara sauki sannan Allah ya tsareki daga sharrin abin ƙi ni zan wuce!”. A hankali Mommy ta ɗan yunƙura tare da lumshe Idanunta kana tace. “Ameen ya hayyu ya ƙayyum Hajiya Ruƙayya Nagode”. Hajiya Lami da Hajiya Bunayya kuwa baki suka saki suna kallon Hajiya Ruƙayya da Mamaki aransu suka ce kaji shegiyar mata da iyayi uban wa takewa wannan addu'ar. Miƙewa Raudat tayi tare da riƙe hannun Hajiya Ruƙayya tace. “Aunty Ruƙayya ni zan biki gidanki, Inje in kwana dasu Salman tun da gobe babu makarata”. Da sauri Khausar ta kalli Raudat dake riƙe da hannun Aunty Ruƙayya tace. “Ayyah Raudat am baza mu kwana ba?”. Girgiza kai Raudat tayi tare da langwaɓar da kai kana tace. “ Ni dai Ina tsoro ni bazan zauna ba”. Kai Khausar ta gyaɗa da faɗin. “Shikenan kibi Aunty Ruƙayya”. Murmushi Aunty Ruƙayya tayi tare da jan hannun Khausar dake cikin nata Har sun kai ƙofa Hajiya Bunayya ta ƙirƙiri murmushi tana kallon bayan Raudat tace. “Oohhh Raudat ba zaki bini mu tafi gida ba?”. Kafaɗa Raudat ta maƙale tace. “A'a ni zanbi Aunty Ruƙayya”. Aunyty Ruƙayya kuwa jan hannun Raudat tayi suka fice batare data sake jiran jin Abinda Hajiya Bunayya zata ceba. Bayan tafiyar Aunty Ruƙayya babu da ɗewa Hajiya Bunayya ta miƙe tare da kallon Mommy tace. “Toh ƙanwata zamu wuce Allah yaƙara sauƙi”. Murmushi Mommy tayi da faɗin. “Nagode Yaya ahuta gajiya”. Hajiya Lami tace. “Babu Gajiya”. Sannan suka fice Khausar kuwa jinginar da kai tayi kamar mai bacci. Da daddare Khausar ta miƙe daga kan dogon kujeran asibitin da take kwance ta dubi Mommy da bacci ya fara fisgarta tace. “Mommy”. Buɗe idanu Mommy tayi tare da kallon Khausar tace. “Na'am Khausar ya akayi?”. Ajiyar zuciya Khausar ta saki tana wasa da yatsun hannunta tace. “Mommy baki zargi perpesoup ɗin nan da kika ci azubewar cikin nan ba!?”. Sosai Mommy ta tsira mata ido na second uku zuwa biyar sai kuma ta miƙe daga kwanciyar da take Atake fara'ar dake fuskanta ya gushe cikin ɗaure fuska cikin kakkausan Murya tace. “Khausar!, Khausar!!, Khausar!!!, Ki cigaba Nagode da abinda kike min Khausar, duk irin tarbiyyan da nake baki fatali kike dashi ko, kina ɗaukar rashin yarda kina ɗaurawa mutane ki sani Manzon Allah (S.A.W) Yace. :Azzana zambu walau kana haƙƙun”. Khausar kuwa ƙasa da kai tayi hawaye masu zafi suka cika Idanunta shin sai yaushe mahaifiyarta zata amince da gaskiyar da take so ta sani akan Hajiya Bunayya basa ƙaunarta cutar da ita suke sonyi. Cikin sanyi murya tare da rauni gami da ban haƙuri tace. “Shikenan Mommy kiyi haƙuri Allah ya huci zuciyarki”. Mommy bata tanka taba ta juya ta gyara kwanciyar, ta itama Khausar juyawa tayi ta kwanta zuciyarta babu daɗi. Washe gari Alhamis Da safe Dr ya shiga ya basu sallama dan jikinta yayi sauƙi Sosai Lamiɗo da kansa yaje ya maido su gida. Suna dawowa Hajiya Bunayya ta shigo hannunta riƙe da babban Warmers da tayi Perpesoup ɗin Kaji ta shigo dashi. Zama tayi akan 2sitter tace. “Sannu ƙanwata ya ƙarfin jikin?”. Mommy tayi yar dariya tare da faɗin. “Jiki yayi sauƙi Yaya sai faman hidima kike dani kamar wacce tayi haihuwar farko?”. Dariya Hajiya Bunayya tayi da faɗin. “Ai mai ɓari yafi son akula dashi fiye da mai haihuwa”. Khausar dake tsaye duk takaici ya gama cikita gashi babu dama ta faɗawa mahaifiyarta gaskiya sai ta hau kanta da faɗa bayan da ta iya daga ƙarshe ma Saboda takaici kawai sai ta koma Bedroom ɗin ta ta fara karatu. Wunin ranan haka Hajiya Bunayya ta yini tare da Mommy ta cigaba da kulawa da ita. Washe gari juma'a dai-dai lokacin da maza suka tafi Juma'a dai-dai lokacin da kowa ya tafi Sallar juma'a Akuma lokacin ne Hajiya Bunayya da Hajiya Lami suka tafi gidan Boka Kar'uzu. Khausar da Mommy ne zaune suna hira sosai jikin Mommy yayi ƙarfi abinka da mai juriya ga kuma kulawa da take samu. Sallamar Aunty Ruƙayya ya katse musu hirar da suke. Khausar ta faɗaɗa fara'ar fuskarta kana tace. “Aunty Ruƙayya sannu da zuwa ina Affan?”. Murmushi Aunty Ruƙayya tayi tana zama tace. “Affan yana lafiya bacci ma yake ya mai jikin”. Khausar tace. “Jiki da sauƙi”. Aunty Ruƙayya tace. “Masha Allah Ubangiji ya ƙara sauki”. Cikin sakin fuska Mommy ta gyara zaman hular dake kanta tace. “Hajiya Ruƙayya sannu da zuwa ya gajiyarki?”. “Hajiya Ruƙayya tayi murmushi da faɗin. “Babu gajiya ya jikin naki?”. “Jiki yayi sauƙi ya yara?”. Alhamdulillah ta bata amsa. Khausar kuwa miƙewa tayi cikin neman izinin tace. “Ayyah Mommy zanje gidan su Asma'u?”. Ido Mommy ta zuma mata, na tsawon second bakwai tana kallonta kana tace. “Toh yayi kyau”. Khausar kuwa juyawa tayi ta shiga Bedroom Dogon rigar dake jikinta ta cire tare da ɗaura towel tashiga toilet, shawer ta ɓude ta sakarwa kanta ruwan ɗumi, ta ɗauki kusan minti shabiyar kafin ta fito ɗaure da towel da tsawon sa bai wuce gwiwar taba yayin da ƙarami ke kanta tana tsane ruwan kanta. Stool ta janyo ta zaune tare da goge ruwan jikinta ta ɗauki Vassiline lotion ta shafa kana ta ɗauki powder ta shafe sai kuma Kajol ta zizara a idanunta mascara ta ɗauka ta taje gashin Idonta da sukayi tsayi tamkar tasa Eyelashes golb mai sheƙi ta ɗauka ta shafa asaman pinch lips ɗin ta sai yayi kamar jan baki ta shafa kallon fuskarta tayi a mirrow sosai tayi kyau. Miƙewa tayi ta nufi jikin durowar ta buɗe uban kayan dake ciki ta zubawa ido ahankali Idanunta suka sauka akan wani Less Coffee da aka masa adon cycle da rastin Milk colour ta janyo ta sanya Masha Allah Sosai ɗinkin less ɗin ya mata kyau tare da fitar da shape din jikinta skirt ɗin ya zaune ɗass ajikinta tare da fitar mata da tsarerrenn ƙugunta haka ma rigar ta zauna ɗass ajikinta ɗan kwalin ta ɗauka tayi ɗauri mai kyau sai kuma ta ɗauki glaye medium size milk color kana ta feshe jikinta da turarukanta masu daɗin ƙamshi. Falon ta fita tun kan ta isa Aunty Ruƙayya ta ɗago kanta tare da tsira mata Idanunta jin ƙamshin daya ratsa hancinta ta saki murmushi kana tace. “Iyeee Masha Allah Khausar irin wannan kyau sai kace preety ta ƙasar India”. Hannu Khausar ta sanya ta rufe fuskarta tana dariya sai kuma ta buɗe tace. “Kai Aunty Ruƙayya Ina Zan samu koda rabin kyawunta ne?”. Ware ido Aunty Ruƙayya tayi kana tace. “Allah kuna kama dan da zakije India ma cewa za'ayi ke ƙanwarta ce, har rawan kanki ma irin natane a Film ɗin Chori-Chori Cubke-Cubke ne”. Mommy Kam murmushi take musu batare da tace komai ba. Khausar kuwa Murmushin jin daɗi tayi tare da tsugunnawa ta ɗauki wayar Mommy tace. “Mommy zan tafi da wayarki". Kai kawai Mommy ta gyaɗa mata sannan ta ɗauƙi wayar tare da faɗin. “Na tafi”. ta ida maganar tana gyara zaman Handbag din Hannunta tare da ciro earpiece aciki Suka haɗa baki wajen faɗin. “Adawo lafiya". Kai ta jinjina tare da ficewa, Abokin gate ta haɗu da Haiydar riƙe da MP ɗin sa, cikin sauri tace. “Yauwa Haiydar dan Allah aramin MP ɗinka”. Cike da mamaki ya zuba mata ido tare da cewa. “Yau kuma to ke kuma da ba jin kiɗa ya dameki ba, me zakiyi dashi?”. Kai ta ɗan jinjina tare da cewa. “Wallahi yau dai shauƙi nakeji zanje wurin Asma'u mu ɗan rausaya”. Murmushi yayi yana mamakin wai yau Khausar ce da cewa zata sha ƙiɗa, kawai miƙa mata yayi. Tare da cewa. “Kuma kikasa gyale ko?”. Cikin daɗi tace. “Ngd kai rabani kullum mutum liƙe da hijabi kamar maitakaba” na mgnar tana fita ta tari adaidaita sahu ta shiga. Acan ɓangaren Moddibo kuwa bayan an idar da Sallah juma'a ya kalli M Jameel dake Driving yace. “J yakamaya muje mu gaida Ummi kafin mu koma gida!”. Kai ya Jinjina kana yace. “Dama abinda nake son faɗa kenan ka rigani”. Gyara zama Moddibo yayi tare da lumshe idanunsa yana sauraron ƙira'ar dake tashi amotar kana ya shafa sajensa yace. “Muje toh”. Kai M Jameel ya gyaɗa tare da juya akalar motar zuwa unguwar su Ummi. Suna cikin tafiya wayar M Jameel ya hau ruri yana duba screen ɗin wayar yaga Bahrain ba suna sai Number Dariya M Jameel yayi still hankalinsa nakan Driving din yace. “Jalaludden! Wallahi Jalaludeen!! nayi mana abinda ransa keso”. Moddibo da Idanunsa ke lumshe yayi ɗan guntun Murmushi ba tare daya buɗe idanun ba yace. “Toh ka ɗaga mana kar ya yanke”. Picking M Jameel yayi tare da Sallama. Amsawa Jalaludeen yayi da faɗin. “Idan kun isa ku gaishe da Ummi”. M Jameel yayi Murmushi kana yace. “Kana biye da mu ne?”. “A'a bana biye daku na dai rigaku zuwa na gaisheta”. Cewar Jalaluddeen Dariya M Jameel yayi sai kuma ya zare ido yace. “Wallahi Jalaludeen kada ka razana mana tsohuwa!”. Murmushi Jalaludeen yayi yace. “A'a bazata ra zanata ba sannan ba zata tsorata ba ai mun taɓa zuwa tare daku baku dai sani bane kuma na bayyana mata ta ganni”. “Wallahi Jalaludeen ka kiyaye mufa”. Dariya Jalaludeen yayi kana yace. “Tare dai mukayi sallama jumma'a a sahu daya. Yanzu kuma Na dai hango ku ahanya zakuje yanzu ina katakon nan?”. Da sauri M Jameel yace. “Wani katakon?”. Cike da tsokana Jalaludeen yace. “Katakon dake gefenka”. Murmushi M Jameel yayi tare da kallon Moddibo yace. “A.J ɗin nawa ne katako?”. “Eh inba katako ba shi menene? ka faɗa masa cewa akwai furen dake ƙoƙarin tsiro a jikinsa tun daga ƙasa har ya isa zuciya ya gab da kanshi tuni ma ya ratsa zuciyarsa amma bai sani ba”. Murmushi M Jameel yayi tare da kallon Moddibo da still Idanunsa ke lumshe kamar mai bacci kana yace. “Wai yace in faɗa maka akwai furen da zai fito tsakiyar kanka yama ratsa zuciyarka”. Sai asannan Moddibo ya buɗe idanunsa ya kalli M Jameel tare da faɗin. “Ka ganni karabu dani da kalaman Jalaludeen, shiya sani can yaje yata faman maganganunsa da baza ka gane kansu ba bare gindinsu ya riƙa yi mana maganar damu mutane zamu gane ba sai wanda sai sune masu ganewa ba”. Dariya Jalaludeen yayi yace. “Zaka gane ne ai lokaci ne yana zuwa”. Dariya M Jameel yayi tare da hong aƙofar gidan Ummi ganin shiru ba'a buɗe masu bane yasa, M Jameel fitowa ya buɗe, kana ya dawo yaja motar still kafaɗarsa saƙale da wayar Jalaludeen ne yace. “Ku gaishe da Ummi idan kun shiga”. Sannan ya katse wayar kana shi kuma ya kutsa kai cikin gidan. Dai-dai lokacin da a dai-dai-ta ya ajiye Khausar kudinsa ta basa tare da buɗe ƙaramin ƙofar dake maƙale da gate ɗin tashiga, Batama lura da babban gete ɗin dake ɗan buɗe ba, ganin mota a fake a harabar gidan yasa ta isa wajen kasancewar glass ɗin tink-tenk ne yasa bata fahimci da mutane aciki ba rawar kanta kuma ya hanata fahimtar alamun yanzu motar ta tsaya. Jikin gefen mai zaman banza ta nufi tare da kallon fuskarta ajikin mirrow sai kuma ta juya manyan Idanunta kalaman Aunty Ruƙayya suka dawo mata kunne tana kama da Preety matsa pinch lips ɗin ta tayi tare da lasa kadan sai kuma ta juya manyan Idanunta. M Jameel kuwa dake mazaunin Driver murmushi ya saki domin ya tabbata bata san da mutane aciki ba. Acan ɓangaren su Hajiya Bunayya kuwa zaune suke gaban boka Kar'uzu cikin tsananin ɓacin rai da fushi Boka Kar'uzu ya buga musu wata razananniyar tsawa cikin sautin muryarsa mara daɗin sauti bayan ya gama sauraron Hajiya Bunayya yace. “Ai seda na faɗa muku aduk lokacin data fara aiki da maganin kada tayi alwala da sallah na tsawon wata ɗaya amma saboda taurin kai kuka bari tayi alwala tayi sallah shiyasa yake kallon fuskar ta kamar na ƙonennen Biri”. Atsorace Hajiya Bunayya ta juya ta kalli Hajiya Lami da itama ɗin Iran take kallo. Sun kasa hafimtar sharrin boka na wasa da hankali da ƙarya sun kasa tuna sam bai faɗa musu hakanba a lokacin, su kasa aminta mgnar boka dubune babu gsky ko ɗaya sai yaudara da taɓewa. Acan ɓangaren su Moddibo kuwa sake kallon madubi Khausar tayi tare dasa hannu ta gyara man lips ɗin ta sai kuma danna MP ɗin cikin Sa'a kuwa sautin waƙar BUGA ya fara tashi. A hankali ta gyara tsayuwar ta, tare da fara jujjuya ƙugunta a hankali tana mai rausaya jikinta. Zuwa tsakiyar waƙar kam fa da abu ya jiƙa, sai ga mayafinta bisa kafaɗarta gefe ɗaya, sosai take jujjuya mazaunenta tare da motsa dukkan jikinta, tana mai kallon kanta a madubi. Sai kuma ta kalli Glass ɗin tare da ɗaura bakinta akai ta saki zazzafan kiss muahhhh. Shi kuwa Moddibo dake zaune idanu ya zuba mata tare da manna kumatunsa adai-dai glass ɗin sai kuma hakan yasa lips ɗinta sauƙa kan....! FREE page sun kusa ƙarewa 0661110170 GTBank AISHA ALIYU GARKUWA ki biya 1k dinki ya isheki By *GARKUWAR MARUBUTA* [19/07, 7:44 PM] Halimatu A/rahman Sadeeya: 📝✨💫⏰🤴🏻👹❤️❤️❤️🍇 *SAKAYYAH* _Page 12_ _NA_ *AYSHA ALIYU GARKUWA* 🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 *Littafin SAKAYYAH na kuɗine wannan Free page ne ƴar uwa ki biya ki karanta cikin Aminci 1k ne kacal 0661110170 GTBank AISHA ALIYU GARKUWA sai ki turo min shaidar biyanki ta WHATSAPP 09097853276 saura shafi huɗune kacal ana biyar na gama Free page* Da sauri Modibbo ya rintse idanunsa, tare da shafa sajensa domin, badan glass dake tsakani ba da akan tattausan sajensa sumbatar zata sauƙa. Shi kuwa M Jameel cikin sauri ya lumshe idanunsa tare da gyara zamansa yana fuskantar ta da kyau. Ita kuwa Khausar hannu tasa tare da gyara zaman ɗaurin ɗan kwalinta, sai kuma ta canza Baitin da take ji zuwa. Waƙar Lamba tana marming tamkar zabia kai kace itace ta raira waƙar, bin baitukan takeyi tana jujjuya manyan idanunta, tana mai girgiza jikinta zuwa ƙugunta. lumshe manyan Idanunta kumayi tare da fitar da sautin zazzaƙar muryanta a fili ta tace. “Kai zan yiwa kalamaina. Kai zan baiwa muƙamai na. Ungo makullaina ka riƙe. Ta ida bautin tare da nuna saitin fuskar Moddibo da yar yatsarta ma nuniya. Wani irin shu'umin murmushi M Jameel ya sake tare da sa hannunsa ya riƙon hannun Moddibo da ya yunƙura zai ɓalle karfin motar. Ita kuwa Khausar, cikin azama taci gaba da bin waƙar cike da zazzafan shauƙi tace. “Ni ban furta da wasa ba, samari dukka basu kai ba, kana nan banganin kowa da ido, dan basu isheni kalloba”. Tayi mgnar bisa alamu daga ainihin cikin ranta take bin waƙar, M Jameel kam murmushi yakeyi cike da shauƙi. Modibbo kuwa ya cika yayi fam dan har ransa yakeji yarinyar ta tarainashi gani yake kai tsaye ma dashi takeyi, gashi kuwa M Jameel ya riƙe masa hannunsa ƙam-ƙam. Ita kuwa Khausar mazari uwar rawa, ƙugunta da ƙirjinta take motsawa a slowly tana mai ci gaba da cewa. “Kai zaka zauna adamana, kuma ka bani gurin kwana, wannan shine fassarar mafarkin da nake kullum cikin baccina”. Wani irin yar-yar Moddibo yaji tsikar jikinsa na tashi domin suna jinta ras kasan cewar Glass ɗin bayan motar a suna ƙasa kaɗan. Ita kuwa Khausar ida baitin tayi tana mai nuna Moddibo dake kwance jikin kujeran Idanunsa alumshe da yatsan hannunta tana murmushin dake ƙarawa fuskarta kyau. Shi kuwa Moddibo Cikin fushi ya fuzge hannunsa daga riƙon da M Jameel yayi masa tare da sanya tattauaan tafin hannunsa da niyyan buɗe motar. Shi kuwa M Jameel cikin sauri ya riƙe tafukan hannunsa da ƙarfi tare da girgiza masa kai alamar ya bari suga iya gudun ruwanta. Ƙwafa Moddibo yayi tare da jingina bayansa da jikin kujeran ya cigaba da kallonta. Ita kuwa rawanta ta cigaba dayi tana Girgiza jikinta ganin abin nata ba mai ƙare wa bane yasa Moddibo buɗe motar cike da tsananin fusata. Kamar walƙiya ko wanda ya diro daga sama haka taga Moddibo a gabanta, Cikin tsoro, mamaki, da kiɗima kalli fuskarsa cikin zare ido ta tayi ƙasa da kanta, domin bata tsammaci da mutum aciki ba. Shikuwa Moddibo cikin nutsuwarsa da kuma kamala ya fito daga motar tare da tsaida idanunsa akanta yana mai ƙara tsananta suƙe fuskarta da ya ƙara razanata. Ita kuwa cikin tsananin ruɗu da tashin hankali mara misaltuwa ta ɗaura hannunta akai. tare da zubewa akan gwiwoyinta tana mai girgiza kanta gaba ɗaya ta gaza cewa komai. M Jameel kuwa gefen Driver ya buɗe tare da fitowa yana dariya mai sassayan sauti, dai-dai lokacin da Ummi da Asma'u suka fito daga cikin gidan zuwa harabar gidan. Idanu Ummi ne suka sauƙa akan Moddibo da M Jameel kafin kuma ta maida ganinta kan Khausar dake durƙushe ta kama kai da hannunta duka biyu, cike da mamaki asaman fuskarta Ummu tace. “A'a ikon Allah Khausar lafiya ya dai haka!?”. Kasa cewa komai Khausar tayi, still hannunta na kanta haka zalika ta kasa ɗago kanta banda bugawa da ƙarfi babu abinda zuciyarta keyi da ƙarfi. Ganin Ummi da tambayar da take yiwa Khausar yasa Moddibo basarwa kamar baisan da ruwan ɗigon Khausar dake tsugunne gabansa ba, cike da nutsuwa da kuma takun ƙasaita ya janye ƙafarsa da ya ɗaga da niyar zaiyi wasan ƙollo da Khausar ɗin yana mai maida fushinsa ya haɗiye ya juya ya nufi gaban Ummi. Murmushi Ummi tayi Idanunta akan Moddibo tace. “Sannun ku da zuwa Babana, dama yanzu nake shirin zuwa unguwa zanje duba jikin Maman Khausar”. Ta ida mgnar ta maida kallonta kan Khausar da har zuwa yanzu take durƙushe sai dib dab dib dab da sautin zuciyarta ke badawa, cikin kula tace. “A'a Khausar yaushe kika zo? ya jikin Mommyn ki?” Ita dai Khausar bata ɗago ba bare kuma ta motsa, gani take aduk lokacin da tayi kuskuren ɗaga kanta Moddibo zai iya kifeta da azabebben marinsan nan mai sa mutum ganin taurari masu wutsiya. Cikin kula Ummi ta juya ta kalli Moddibo dake tsaye hannunsa na acikin aljihu murmushi tayi kana tace. “Allah yayi zaku zo ku sameni, kuzo mushiga daga ciki”. Kai suka jinjina tare da wuceta, ita kuwa Ummi juyawa tayi zuwa gaban Khausar ɗan tsugunna tayi tare da riƙo hannun Khausar tace. “Duk cikin gaishe da Malama ne har haka Khausar? to taso mu tafi”. Sai asannan Khausar ta ɗago kanta tare da sakin wani nan-nauyan ajiyar zuciya, ganin Moddibo bai nan cikin mutuwar jiki tabi Ummi falon. Suna shiga Khausar tayi saurin janye hannunta daga cikin na Ummi, kana ta kama na Asma'u suka nufi Bedroom ɗinta”. Suna shiga Bedroom ɗin Khausar ta janye hannunta daga na Asma'u ta zauna agefen gadon Idanunta cike da ruwan hawaye ta dafe ƙirjinta tare da cewa. “Asma'u nashiga ukuna!nikam yau naga ta kaina, Allah yana jarabtana ta hanyar haɗani da Moddibo a bauɗaɗɗen yanayi, zuwa na kenan naji wata waƙa tamin daɗi na tsaya ina bi uwa zabiya. Kuma kin sanima fa ni ban fiye jin waƙa ba, sannan bai dameni ba amma kawai ɗazu naji wata waƙa MP din Haiydar Wai ita Buga da Lamba kuma wallahi nasan Haiydar ne ya haxa min da bai bani aron MP ɗinsa ba ai da banjita ba bare inji yamin daɗi, kawai na kama rawa tamkar yar gala, ashe Moddibo na kallona nikam bansan irin hukuncin da zai minba gobe amakaranta, ƙilan ma ya sake sakani kaɗe ɗan kwali nikam nashiga Ukuna! Laifi kan laifi gashi gyale na yafa ga uban turaren dana zumbuɗa ga rawa dajin waƙa Wayyo ni Batula Faɗimatuzzahara naga ta kaina!”. Ta gumi Asma'u tayi tare da kallon, Khausar da tayi narai-narai da ido kana tace. “Ke kam dai Khausar kamar saɓani Allah yake haɗaki dashi”. Narai-narai tayi da ido tare da dafe kuncinta da hannun biyu kana tace. “Mummunan saɓani ma kuwa, na sharri ma ya Allah kashiga tsakanin na gari da mugu, Allah kara bani dashi ya Allah kada ka bashi ikon zalunta na, tun da dai arashin sani nayi kuma babu wanda yafi ƙarfin kuskure ai seya min uzuri ko?”. Janye mata tagumin Asma'u tayi tana dariya tace. “Kece Khausar wani zubin sai ahankali, kawai daga zuwa saiki hau rawa kamar mazari da anyi magana ki wani ce Allah yashiga tsakanin na gari da mugu sannan da kike maganar uzuri a'a ba'asi za amiki ba uzuri ba kuma waye mugun waye na garin”. Sheƙeƙe Khausar ta ɗago kai tare da tsirawa Asma'u Idanu kana tace. “Nifa na lura dake tun ba yanzu ba, kinfi ƙaunar Moddibo dani wato har kina goyon bayan sa akan ni kin zaɓe sa kin barni? Yoh shine mugu mana ni ta gari”. Ware idanu Asma'u tayi tare da langwaɓar da kai tana dariya tace. “Haba ƙawar arziƙi matsayinki yafi haka, dan Allah kada ki sake faɗan hakan aise kisa ayimina dariya”. Taɓe baki Khausar tayi tare da faɗin. “Kinsan gwara in gane matsayina ai tun wurima, idan kinfi ƙaunar Moddibo insan matsayina”. Dariya mai sauti Asma'u tayi da faɗin. “Maida wuƙar ranki shi daɗe Fattanah”. Murmushi Khausar tayi tare da kishingiɗa akan gadon. Acan falo kuwa bayan Moddibo da M Jameel sun sake gaisawa da Ummi ta miƙe tashiga kichen ba daɗewa ta fito hannunta riƙe da babban tray dake ɗauke da Warmers ta ajiye musu. Murmushi Moddibo yayi yace. “Sannu da gajiya Ummi”. Murmushi tayi tace. “Yawwa Babana”. M Jameel kuwa miƙewa yayi yashiga kichen ya dauko musu Plate da cups guda biyu kana ya dawo ya zauna. Kulan ya buɗe, da sauri ya gyara zamansa jin wani ƙamshi mai daɗin ya ratsa hancinsu. M Jameel ya lumshe ido tare da zuba musu akan Plate. Moddibo ya matso tare da tsirawa Pride rice ɗin da yaji vegetables da naman kaza amsar spoon ɗin da M Jameel ke miƙa masa yayi, cikin fesar da numfashi Moddibo ya ɗibi abincin ya kai bakinsa, lokaci ɗaya yaji daɗi ya mamaye masa baki, kallon Ummi yayi tare da faɗin. “Ummi wannan girkin yayi daɗi”. murmushi tayi tare da tsiyaya musu tea mai ɗumi. Bayan sun gama ci. M Jameel ya goge bakinsa da tissue kana yace. “Ummi ɗazun ina zakije dama?”. Tana matsar da Flaks ɗin tea tace. “Wallahi Maman Khausar zanje dubawa, bata da lafiya shekaran jiya a asibiti suka kwana jiya ne aka sallame su da safe”. Girgiza kai yayu kana yace. “Ayyah Subhanallah Allah yabata lafiya Allah yasa zakkan jikine”. Amin Ummu tace. Yayinda shi kuwa Moddibo Aransa yace. “Uhhhm yarinyar kamar aljana ita da mahaifiyar ta babu lafiya har ankwantar da ita a asibiti jiya-jiya aka sallame su, amma yau har ta gararo yawo, har tana rawa agidan mutane kamar wacce aka yiwa bushara da Aljanna, ita kuwa wannan daɗin me takeji”. sai kuma ya taɓe baki takaicin halayyar yarinya yasa bece musu komai amaganar ba. Ajiyar zuciya ya sauƙe tare da faɗin. “Toh Ummi mu zamu tafi”. Ummi ta juya ta kallesa da murmushi afuskarta tace. “Da wuri haka Babana?”. M Jameel ne yace. “Ai dama a gaggauce muka zo Ummi, dan kwana biyun nan naga ya maida hankalinsa akan rubutun da yake inagama ya kusan gamawa”. Ummi kuwa kallonta ta mayar kan Moddibo kana tace. “Masha Allah Ubangiji Allah ya taimaka, ya kuma baku sa'a ka kusa gama wa kenan?”. Cike da nitsuwa Moddibo ya amsa da. “Ameen”,Kana yace. “Eh Ummi na kusa gamawa, amma waɗan da na tura ƙasar Ɓadamaya ma tukunna wanda na turawa, Sheykh Jabeer ya duba min su har yau basu dawo ba, to inaso kawai na haɗa wa'annan ma dake wancan bugun Hafs ne wannan kuma Warash ne”. Yai da mgnar tare sauƙe numfashi kana ya cigaba da cewa. Warash ne nake rubuta wa to inaso idan nagama rubuta wannan ɗin na tura masa, wala Allah ya tuna mishi da duba wancan ɗin. Nasani abubuwa ne suka masa yawa da yake ya wanci yakin arewacin nan duk wanda ya rubuta Kur'ani shi ya ake turawa sai ya duba yagani toh zanyi ƙoƙari na gama rubuta wannan ɗin sai ahaɗa akai gaba ɗaya ko zan samu ya haɗa min su lokaci ɗaya idan ya duba ingancin su”. Jinjina kai Ummu tayi cike da yabawa jajurcewarsa da kuma ƙoƙarin sa tace. “Masha Allah Allah yatemaka Allah ya bada sa'a abu yayi kyau Allah yabar mana irinku Moddibo Allah yayi jagora”. Moddibo kuwa cikin jin daɗin addu'ar ta yace. “Ameen Ummi Allah ya amsa Nagode”. Miƙewa M Jameel yayi idanunsa akan Ummin sa yace. “Ummi zamu tafi”. Tana ƙoƙarin kwashe Plate da sukayi amfani dashi tace. “Toh Nagode Allah ya muku albarka”. Suka haɗa baki wajen faɗin. “Ameen”. kana suka fice. Bayan sun ɗauki hanya M Jameel ya dubi Moddibo wanda shike Driving ɗin yanzu yace. “Ni ka sauƙe ni agida”. Moddibo da still hankalin sa ke kan Driving yace. “Ba zamu tafi tare ba?”. Girgiza kai M Jameel yayi kana yace. “A'a nasan rubuta zaka je kayi sannan Abba ya kirani akan batun yana so naje Ɓadamaye batun Company sa akwai sabbin Injina da aka kawo, za'a saka kaga na daɗe ban jeba, amma wannan karon ko naje baze wuce kwana biyu zanyi in dawo ba”. Moddibo kuwa jinjina kai yayi kana yace. “Toh yaushene tafiyar?”. Kai M Jameel ya Girgiza tare da faɗin. “Toh dai ban sani ba tukun”. Moddibo dake ƙoƙarin shan kwana yace. “Yawwa zanyi ƙoƙari inga na gama rubutunan idan zaka tafi sai ka tafi min dashi”. Shi kuwa M Jameel Kai ya gyaɗa cike da gamsuwa da maganarsa yace. “Toh shikenan hakan ma yayi Allah yatemaka”. Moddibo ya amsa da. “Ameen”,tare da parking motar bayan ya isa ƙofar gidan su M Jameel. Sauƙa M Jameel yayi tare da yi masa sai anjima, kai Moddibo ya gyaɗa kana yaja motar ya tafi. Yana isa gida bayan yayi Parking motarsa ya wuce Bedroom ɗinsa kasancewar yana da alwala yasa ya ɗauko abubuwan buƙatar sa na rubun Alkur'ani da yakeyu kana yaciigaba da rubutu, saida aka kira sallar La'asar sannan ya tashi yaje masallaci ya gabatar da sallan la'asar, bayan ya dawo kuma, yazo ya cigaba da rubutun, yana yi yana karantar Suratul Kahfi kasancewar yammacin jumma'a ne, sai misalin ƙarfe biyar kafin ya ajiye Kur'ani. Acan ɓangaren Innayi kuwa zaune take akan kujera ’yar tsugunno acikin kichen tana juya miyar zogala wanda yaji namar Rago da kuma wadataccen man Shanu da wake yana tashin ƙamshi bayan ta sauƙe miyar ta ɗaura Ruwan shayi daya ji na'ana, kaninfari da kuma ɗanyan citta yana tafasowa yana ƙamashi mai daɗin shaka. Flaks guda biyu ta ɗauka ta juye sannan ta ɗauki ɗaya ta nufi sashen Moddibo dashi. Acan gidansu Asma'u kuwa bayan tafiyar Moddibo da M Jameel Khausar ta miƙe tare da fitowa falon Idanunta akan Ummi tace. “Toh Ummi mu tafi ba dama kince gidan mu zaki jeba”. Jinjina kai Ummi tayi tace. “Eh Khausar inaso naje na duba jikin Mommyn ki”. Ba tare data zauna ba tace. “Toh Ummi mu tafi”. Kai Ummi ta jinjina kana ta miƙe suka fita su ukun Bashir ƙanin Asma'u ne kaɗai suka bari agida Ummi da kanta take Driving Khausar da Asma'u na baya suna hira. Acan ɓangaren su Hajiya Bunayya kuwa Kallonsu Boka Kar'uzu yayi cikin wata razananniyar tsawa yace. “Wannan maganin ya riga daya ɓaci, ta lalata komai yanzu sai anyi aikin dai-dai-ta fuskarta ma tukunna kafin azo ayi aikin jawo hankalinsa, yaran nan biyu da kuka gani kuke magana akansu yarane dasu na tsaye da sunan Allah da riƙo da Ibada, musamman ma Moddibo da kuke magana akansa kwata-kwata baya rabuwa da alwala ajikinsa ka masa zaiyi wuya”. Cikin tashin hankali Hajiya Bunayya ta juya ta kalli Hajiya Lami da duk tagama shiga ruɗu. Boka Kar'uzu kuwa cigaba yayi da cewa. “Yanzu sai munyi aikin wata uku kafin fuskarta ya dawo dai-dai sannan sai tabar Sallah na tsawon watanni shida kafin mu samu mu fara aiki shiko aikin za'ayi na tsawon watanni shida kafin ta fara nuna masa muradanta”. Kana ya maida kallonsa ga Hajiya Lami data zabga uban tagumin tana kallon sa cikin Muryansa Mara daɗin Amo yace. “Kema naki hakanne sai tayi wannan watannin”. Dafe ƙirji Hajiya Lami tayi tare da zare Ido kana tace. “Har Watanni shida shida Boka kafin wannan lokacin fa har sun kusa gama Ss 2 ma zasu tafi 3 awannan lokacin daka ɗiba mana”. Cikin tsawa da hargagi yace. “Dole sai anbi wannan ƙa'ida idan ba haka ba babu abinda zaku samu ya tafi dai-dai!”. Ta gumi Hajiya Lami ta rafka kana tace. “Shikenan Babu damuwa Indai burinmu zai cika tunda ai makarantar basu gama ba zamu bi ahankali”. Ya yamutse fuska tare da watsa musu wani kallo da jajayen Idanunsa cikin wata murya mara daɗin Amo yace. “Ƙa'idah ne yanzu zata je tayi ta aiki da wannan maganin na tsawon watanni ukku fuskarta zai koma dai-dai a Idanunsa sannan bayan wannan kuma tsawon watanni kar kuyi sallah daga nan kuma zan fara haɗa magani na tsawon watanni shida kafin su tun kare su daga magana”. Murmushin Hajiya Bunayya tayi tare da gyara zamanta tana fuskantar Boka Kar'uzu da kyau tace. “Toh shikenan ba matsala. Amma fa ciki ya zube aiki yayi kyau!”. Wani irin mahaukaciyar dariya mai matuƙar razanarwa Boka Kar'uzu ya saki da faɗin. “Ai dama dole aiki zaiyi kyau idan kun bishi da ƙa'ida wannan ma ku kuka je kuka ɓatashi!”. Jinjina kai Hajiya Bunayya tayi tare da cewa. “Godiya muke Boka ana gaba zamu kiyaye”. Kai ta gyaɗa kana yace. “Toh ya batun aikin toshe mahaifar!?”. Kai Hajiya Bunayya ta Girgiza tare da faɗin. “Boka muga ma da batun aikin Amina tukunna, kaga ga yayar ta ma tana zaune ba tayi aure ba, sannan ga itama Aminan ta girma shiru, amma ita kace rabonta ne yayi nisa abin ya ɗaure mana kai mun rasa yanda zamuyi har wajen ƙan wata na tura ta Aƙasar Khautal ko zata samu rabonta acan amma acan ɗin ma shiru kuma kaga ta dade da gama karatu amma har yau Auren bai samu ba zamu jona mata wani makarantar ta fara zuwa jami'a kawai, tunda itama kanta Amina dan wasa da karatun take da tayi shekaru biyu da gamawa amman sai aikin maimaita aji gashi har shegiyar yarinyar nan ta kusan cimmata”. Kai Boka Kar'uzu ya ɗago daga bugun ƙasar da yake tare da cewa. “Babu matsala ita Aseeya rabonta yana nan tafe”. Cike da jin daɗi Hajiya Bunayya tace. “Godiya muke Boka Uban bokaye La'anannen Uban La'anannu Mugu Uban mugaye Hatsabibi Uban Hatsabibai!”. Wata mahaukaciyar dariya Boka Kar'uzu ya kece dashi cikin jin daɗin kirarin da ta masa yace. “Aikin ki zai tabbata ƙaramar la'ananniya Aljani ɗan ƙundalu mai ido Atsakiyar kai zai cika miki burinki ku fita da ƙafar hagu ta baya!”. Miƙewa sukayi suka fice kamar yanda ya faɗa ransu fesss suna tsalle da kafar hagu kamar kutaren agwagi... Acan ɓangaren su Ummi kuwa bayan sun isa gidan su Khausar sun gama gaisawa da Mommy da kuma Hajiya Ruƙayya da har zuwa lokacin suke tare. Mommy tana murmushin tace. “Ummi ya fama rigimar Khausar, ɗazun nan tace zata je ta duba ki ashe kina hanya”. Dariya Ummi tayi tace. “Ai lalle dai kam Hajiya Aysha babu ruwan Khausar ai”. Murmushi Mommy tayi tace. “Kina dai karate ta Amma Khausar ba dai rigima ba?". Aunty Ruƙayya tayi Dariya kana tace. “Ai Khausar bata da rigima ita dai baza'ayi gulma agaban Idanunta bane, sannan ba za'a cakake ta ta haƙura ba, kunga kuwa ai da gaskiyar ta”. Dariya Ummi tayi tace. “Aikam de lalle da gaskiyar ta”. Ita kuwa Mommy Dariya tayi kana suka cigaba da hira. Washe gari Asabar suka koma makaranta Khausar kuwa cikin tsoro da fargaban abinda Moddibo zai mata ta zuciyarta ya riƙa bugawa da ƙarfi lokacin da yashigo raba musu questions pepar tayi zaton zai mata hukunci sai taga baima kalli inda take ba. Shikuwa Moddibo kawai ya fita sabgarta ne ganin alamar bata da cikikakkiyar nutsuwa in ya biyata zata zarar dashi. Akwana atashi haka al'amura suka cigaba da tafiya komai yana wakana Moddibo ya kammala rubutun Kur'aninsa ya bawa M Jameel ya tafi wa da Sheykh Jabeer Habibullah Nuruddeen Joɗa na Adamawa. Satin M Jameel biyu ya dawo tare da shedawa Moddibo ya karɓa harma ya fara dubuwa Insha Allah nan kusa zai turo masa. Karatun su Khausar na tafiya komai na tafiya dai-dai yanda ake buƙata Anyi gasar musabaƙa jihar Taraba Makarantarsu Khausar Al'ansar Academic school_ shine yazo na farko Khausar ce tazo na ɗaya a haddar Izu arba'in yayin da Asma'u tazo na biyu Aishatu Abdullahi tazo na uku ,A haddar Izu biyar Raudat ce tazo na ɗaya kyaututtuka masu yawa suka samu kana suka dawo cike da nasarori. Yanzu karatu na tafiya akwana atashi babu wuya wasa gaske yanzu Khausar suna Ss2 thirth term suna shirye shiryen fara Exam gashi kuma Ramadan ya kawo kai yayin da ake ta shirye shiryen shiga Ramadan tuni Gwamnatin Jaha ta rarraba malamai zuwa inda ko wanne zaiyi Tafseer kamar yanda aka saba Moddibo da M Jameel antura su Babban Masallacin juma'a dake ƙofar sarki Gembu anan zasuyi Tafseer ɗin su na Ramadan. Lokaci natafiya karatun su Khausar na sake tafiya yanda ake buƙata tsakanin Amina da Khausar babu wani jituwa hasalima gaba ce domin har gobe M Jameel na sake nuna kulawa ta musamman akan Khausar yayinda Moddibo kuwa kwata-kwata baya lura da al'amuran Khausar hasalima idan tayi laifi zai yanke mata hukunci fiye dana kowa wannan dalili yasa basa shiri kana babu wata jituwa atsakaninsu. Alhamdulillah ayaune Khausar suka rubuta exam na ƙarshe kuma da Geography suka rufe. Taro Moddibo yasa aka haɗa kamar yanda aka saba a kowani ƙarshen hutu ko baki ɗaya Malaman sun haɗu awajen zamansu haka ma ɗalibai Khausar da Asma'u na zaune awaje ɗaya. Shi kuwa Moddibo cikin nutsuwarsa da kuma kamala ya nufo wajen as usual cikin shigar sa kaman ko yaushe sanye yake cikin Jallabiya fari kansa naɗe da hirami idanunsa sanye da ɗan siririn farin glass daya ƙawata kyawun fuskarsa yalwataccen sajensa zuwa gemunsa ya kwanta luf-luf yana sheƙi. Cikin tsantsar nutsuwa da sanin darajar kansa ya gyara zaman microphone ɗin tare da hura iska kaɗan kana yayi gyaran murya yace. _“Bismillahir Rahmanir Rahim, Innalhamdulillah nahmaduhu wanasta'inuhu wanastaghfiru wa'nazubillahi min shururi anfusna wamin sayyi ati a'amalina, man yahdillahu fala mudillahlah waman yudlil fala hadiyala, Wa'ash hadu Allah ilahalillahu, Wa'ash hadu anna Muhammadu Abduhu wa Rasulullah (S.A.W)”._ Sai kuma ya ɗan lumshe idanunsa tare da sauƙe Ajiyar zuciya kana ya cigaba da cewa. “Duk kan yabo da godiya su tabbata ga Allah subhanahu wata'ala mai kowa mai komai, da yakawo mu wannan lokaci da muke shirin karɓan hutu saboda gabatowan wannan wata mai falala, haƙiƙa watan Ramadan wata ne mai falala da rahma wanda duk kan musulmi yake da burin ganinsa. Baki ɗaya wajen shiru yayi kowa ya maida nutsuwarsa zuwa garesa yayin da Samira kejin aduk lokacin data mallakesa babu macen da takaita sa'a a faɗin wannan duniya tamu ta bani adam. Malam Arɗo kuwa Aransa yake jin Moddibo ne Garkuwa kuma ginshiƙin makarantarsa. Moddibo kuwa cikin yanayin sanyin Muryar sa mai cike da nutsuwa ya cigaba da cewa. “An abu Huraira ta radiyallahu anhu, _Manƙama Ramada Imanan Wahtisaban gufra lahu mata ƙaddama min zambi muttafaƙun Alaik”_ Ma'ana ankarbo daga Abu Huraira Allah ya ƙara masa yarda, yana cewa Duk wanda watan Ramadana ya kama yana mai Imani da kyautatawa ana kankare masa zunubansa da suka gabata”. Ya sauƙe sanyayyar Ajiyar zuciya mai sanyi kana ya cigaba cewa. “Wannan kaɗai zai iya nuna maka muhimmanci da kuma darajar wannan wata hakika wannan watar ba wata bane na wasa watane daya kamata mu tsaya mu miƙa lamuranmu ga Ubangiji Mabuwayi gagara Misali, sannan mukasance masu yawan Karatun Alkur'ani, Istigfari, hailala da kuma tasbihi, ba sai na tsawaita ba ko naja duk abinda zance kun sani”. Sai kuma ya maida kallonsa ga sauran Malaman yace. “Koda akwai mai magana?”. Duk suka girgiza kai alamar babu Moddibo kuwa M Jameel ya miƙawa microphone ɗin kana ya koma ya zauna shi kuwa M Jameel bayanai ya ƙara akan na Moddibo kana ya sanar dasu Bayan Sallah da sati ɗaya zasu dawo. Yana gama Maganar ya juya tare da kallon Khausar da ita adai-dai lokacin Idanunta na kasansa cikin Sanyayyar Murya yace. “Lelewal zoki rufe mana da addu'a!”. Anutse Khausar ta gyaɗa kai tare da miƙewa. Shikuwa Moddibo kallon mamaki yabin M Jameel dashi amma baice komai ba. Amina kuwa jitayi tamkar zuciyarta zai buga saboda baƙin ciki da kishi. Ita kuwa Khausar cike da tsoron Modibbo dake sa ta nemo nutsuwa ta amshi microphone ɗin cikin zazzaƙan Muryanta tayi addu'a kana aka tashi kowa ya watse dalibai nata murnan hutu kowa ya koma gidansu cike da farin ciki. Da daddare Khausar na zaune akan 1sitter hannunta riƙe da wayar Mommy yayin da Mommy kekan 3sitter ta miƙe ƙafafunta Hannunta riƙe da kofin tea. Anutse Mommy ta ɗago kanta tare da sauƙe Idanunta dake kan Khausar Wacce baki ɗaya hankalinta ke kan wayar da take dannawa ajiyar zuciya ta sauƙe tare da cewa. “Khausar tunda an baku hutu ko dai za kije Jauro Yaya kuyi azumi tare". Da sauri Khausar ta ajiye wayarta tare dasa hannu ta dafe ƙirjinta tace. “Nashiga Ukuna! Dan Allah dan darajar Annabi Mommy Kar kiyi Wannan maganar, kibar tsohuwar nan tunda dai bata ne maba”. Kai Mommy ta gyaɗa kana tace. “Toh shikenan yanzu azumi saura sati amma nasan zaiyi wuya acikin satin nan idan bata neme kiba”. Marerece fuska Khausar tayi kana tace. “Allah yasa karma ta nemeni duk da garin yamin daɗi Mommy amma inaso in tayaki aiki”. Murmushi Mommy tayi kana tace. “Toh shikenan ba matsala hakan ma Allah ya zaɓa Mana abinda yafi zama alkhairi”. Acan ɓangaren su Hajiya Lami kuwa zaune take afalon Hajiya Bunayya tare da Samira Sani da kuma Amina. Kallon Hajiya Lami Hajiya Bunayya tayi kana tace. “Yanzu dai saura mana watanni biyu mu gama cika Umarnin Boka Kar'uzu na watanni shida daya ɗiba mana kada muyi Sallah, kafin na ƙarshe da zamuyi muje mu karɓi maganin su zo suyi aiki dashi”. Murmushi Hajiya Lami tayi tare da jinjina kai tace. “Eh haka ne bayan Sallah da sati Uku zamu gama”. Jinjina kai Hajiya Bunayya tayi tare da cewa. “Gashi kuma azumi ya gabato amma acikin wannan azumin ma ace ba zamuyi sallah ba kuma watan falala da ibada!?”. Wani kallo Hajiya Lami tayi mata kana tace. “Idan ke zakiyi sallah ki ɓata aikin da kikayi to kinyi na wancan watannin shida da kika samo fuskar ’yar ki ya dawo dai-dai a idanunsa, sannan yanzu wata ɗaya da rabi daya rage ne zaki ɓata ba zaki iya jira ba. Agaskiya nikam zan cika ƙa'idata domin in samu cikar burin ‘yata”. Samira kuwa zama ta gyara tana fuskantar Hajiya Bunayya da kyau tace. “Agaskiya Ummah kar muyi wasa da wannan damar da muka samu idan yaso idan muka gama sai mu rama bashin sallah dake kan mu!”. Ita kuwa Amina Kallon mahaifiyarta tayi tare da ƙanƙance Idanu kana tace. “Yanzu ke Ummah wasa zakiyi da wannan damar da muka sha wahala tsawon watanni muna yi!?”. Zare ido Hajiya Bunayya tayi tare da nuna kanta da yatsa tace. “Ina waya faɗa miki ko an faɗa miki daɗi nake ji ga yayarki azaune gaki kuma kema azaune”. Ta ida maganar dai-dai lokacin da Asiya ta fito daga Bedroom bayan ta gama sauraron duk abinda suke faɗa zama tayi akan 1 sitter dake fuskantar Hajiya Bunayya cikin sanyin murya tace. “Gaskiya Ummah!, Gaskiya Ummah!! Kada neman duniya yasa mu rasa ƙiyama tare da rahamar Ubangiji, Ummah sallah da arayuwar duniya itace farkon abinda za'a bin ciki mutum dashi aranan gobe hisabi idan tayi kyau abin cika sauran abubuwa idan kuma ba tayi kyauba, baza ma aje ga sauran abubuwan ba”. Tayi ƙasa da Idanunta ganin shegen kallonda Umman take bin ta dashi bata damu ba ta cigaba da cewa. “Ummah aduniya Allah ya Umarceki da kiyi sallah da Azumi amma Boka La'anannen yace kada kiyi, sannan ki biye masa har ki yarda sannan ki riƙa ɗaura ‘yarki akan gurɓatacciyar hanya nikam wannan al'amari yana tayar min da hankali, wannan al'amarin sam bai yi ba yanzu dama akan wannan turban kuke tafiya?”. Ta saki Ajiyar zuciya tare da gyara zamanta kana tana ƙoƙarin maida hawayen dake ƙoƙarin zubo mata cikin dauriya ta cigaba da cewa. “Shiyasa tun da na dawo sati biyu banga kinyi alwala ko Sallah ba?, Ni nayi zaton ma al'ada kike yi,Itama Amina naga bata sallah dana tambayeta saita kama yimin rashin kunya”. Amina dake jifanta da mugun hararane tayi saurin katseta tare da cewa. “Anyi miki rashin kunyar keda ba kyabin Ƙa'ida da Umarnin Bokan baga ki har yanzu baki auru ba!sai shegen iyayi da kwainane!”. Asiya da Idanunta suka ciko da ruwan hawaye ta kalli ƙanwar nata cike da mamaki sai kuma tayi murmushi mai ciwo tace. “Wannan Allah ne bai nufaba, idan Allah ya saƙƙo da lokaci zanyi shi domin Aure da mutuwa lokacine”. Atsawace Hajiya Bunayya tace. “Rufe min baki, keda ma can ba'a haɗa shiri dake ya tafi dai-dai, dama ke da magautana kike tare kina nan kamar wancan matar ce ta haifeki”. Asiya ta danne kukan dake neman kufce mata tace. “Ba haka bane Ummah zanso mu gudu tare mu tsira tare ne, bazan so ganin ku cikin halaka ba Umma kuyi tunani akan wannan rayuwar da kuka jefa kanku". Hajiya Lami kuwa cikin fushi tace. “Wannan dai akwai gantalelliyar yarinya shegiya mai shegen mugun halin jaraba, duk yanda akayi wancan gafalalliyar kishiyar Uwar taki ta baki nononta kinsha”. Kallonsu kawai Asiya keyi cike da mamaki. Hajiya Bunayya kuwa Afusace tace. “Bana son gaskiyar taki ki riƙe abarki. ki gudu ke kaɗai mu ma mu gudu mu kaɗai kiga wanda zai riga isa tsakanin mu da ke”. Cikin tsananin tashin hankali Asiya tace. “Innalillahi wa'inna ilahi rajiu'n. Allahumma Ajirni fi musibati wa'ahlif khairan minha”. Ta ida addu'ar tare da miƙewa ta shiga Bedroom ɗin su akan gado ta faɗa tare da dafe kanta tace wannan wani irin Masifa ce Ummah ta jefa kanta. Acan falo kuwa Ummah suka cigaba da tattaunawa tare da tsaida matsaya akan idan sun kammala aiki zasu biya Sallolin da ake binsu. Washe gari. Da hantsi misalin 12:00 Khausar na kwance A Bedroom kamar daga sama tajiyo Sallamar Hajja Nana da sauri ta miƙe tare da zama Atsakiyar gadon ta kasa kunnenta dan tabbatar wa shin ita ɗin ce ko kuwa. Aikuwa Muryan Mommyn ta taji tana cewa. “A'a Hajjar Allah Maraba sannu da zuwa Allah raine Jaɓɓama,Jaɓɓama Yottu,yottu”. Ita kuwa Khausar wani irin zare ido tayi sai kuma ta miƙe da sauri ta fito abakin Bedroom din ta tsaya Idanunta akan Hajja Nana da Dije dake tsaye agefenta. Jan zuciya Khausar tayi tare da tsaida idanunta akan Hajja Nana tace. “Kece?”. Harara Hajja Nana ta watsa mata da faɗin. “Toh ki koreni wato ba kyason ganina!?”. Tura baki Khausar tayi tace. “A'a". Sai kuma ta juya tare da kallon Dije dake tsaye tana kallon falon da dugu ta nufi Dije tana cewa. “Oyoyoo Dije nayi kewarki ya gida ya Goggo Nanne?,Ya Yaya Abba?,Ina Sadik?, Yasu Baffa Jauro?, Baffa Sadu?,Baffa Liman?, Baffa Garga? Ina Bishiyar Ƙare zencen ka ina Rafi?”. Murmushi Dije tayi kana tace. “Duk suna lafiya kuma sunce agaisheki da kyau da kyau”. Tayi murmushi tace. “Allah sarki nima nayi kewarsu sosai”. Cikin sakin fuska Mommy ta fito daga kichen hannunta riƙe da Flaks da kuma kofi biyu ajiyew tayi, kana ta koma ta ɗauko fruits duk ta ajiye agaban Hajja Nana data hakimce akan kujera sannan ta zauna still fuskarta da Murmushin daya kasa ɓoyuwa tace. “Sannu Hajja kunsha hanya ya mutanen gida?” Ta ida maganar tana tsiyaya mata Tea a kofi. Amsa Hajja Nana tayi ta kai bakinta. Mommy kuwa miƙewa tayi ta shiga kichen dan haɗa mata abinci. Hajja Nana kuwa juyawa tayi tare da kallon Khausar dake maƙale da Dije kana tace. “Wato ba zaki gaisheni ba, Dije ce kikayi farin cikin ganinta ni bakiyi farin ciki da ganina bako!?”. Ya mutse fuska Khausar tayi tace. “Tun ɗazu nake ta gaisheki kina fama da ciye-ciye baki jini ba”. Sake baki Hajja Nana tayi tare da riƙe haɓa sai kuma tace. “Ubanki nake baciye-ciye ba” Hannu Khausar ta buɗe da faɗin. “Ɗanki kika zaga dama kin barsa ya kwanta cikin kabarinsa acikin salama da yafi”. Ta ida mgnar idonta na ciko da hawaye dan Allah ya sani bata son a zagar mata mahaifi. Hajja Nana ta ajiye Kofin shayin dake hannunta ta nuna Khausar da hannu tace. “Ki kiyaye nifa,Ki kiyayeni fa Khausar”. Tura baki Khausar tayi kana tace. “To ai gaskiya na faɗa”. Ita kuwa Hajja Nana na ɗaukar kofin shayinta tace. “To ya miki kyau koma mene ki ƙarata can, yanzu kishirya ki haɗa kayanki tare zamu tafi zamu je muyi azumi acan”. Kallonta Khausar tayi kana tace. “Mu tafi ina?”. Hajja Nana tace. “Eh mana Khausar mu tafi Jauro Yaya”. Da sauri Khausar ta maida kallonta gareta kana tace. “To ai muna zuwa hadda”. Hajja Nana tace. “To ai wannan ba abin damuwa bane idan muka je sai Malam Liman ya riƙa ƙara miki”. Kai Khausar ta girgiza kana tace. “Baza ki gane bane, inada abubuwan da zanyiwa Mamana ɗin nan da kike gani ina taya ta aiki”. Hararanta Hajja Nana tayi da faɗin. “Dama kece mai taya ta aikin ina masu taya ta aikin?”. Zare ido Khausar tayi kana tace. “Tayi cikin shege ankoreta ta koma ƙauyensu. Mai gadin muma ana canza shi saboda shi ya mata ciki”. Da mamaki Hajja Nana tace. “Ash'sha Subhanallahi ashe gidan naku babu tsaro kenan, ashe ku gidan bayan maita hadda rashin tsaro a'a maza-maza shirya mu tafi”. Dai-dai lokacin da Mommy ta fito girgiza kai tayi tace. “Kai Khausar bakyajin magana maza ki ɗauka wa Dije abinci ku wuce ɗakin ki”. Kai Khausar ta gyaɗa tare da wucewa kichen ta daukawa Dije abincin sannan suka wuce Bedroom ɗin. Mommy kuwa zama tayi agefen Hajja Nana tare da ajiye mata tiren abinci cikin sanyin murya tace. “Hajja Nana kiyi haƙuri da halin Khausar zaku tafi idan hakan kike so”. Kai Hajja Nana ta gyaɗa kana tace. “Toh babu damuwa amma tace min baki da lafiya da gaske ne?”. Kai Mommy ta Jinjina kana tace. “Eh wallahi kwanakin nan duka ban cika jin daɗi ba bansan meke damuna ba!”. Jinjina kai Hajja Nana tayi kana tace. “Subhanallah Allah ya sawwaƙa Allah ya yaye. Kuma da gaske ne mai aikin ku ta haihu cikin shege?". Dai-dai lokacin Hajiya Bunayya da Amina suka shigo falon. Ɗaga kai Mommy tayi tare da kallon Hajiya Bunayya data zauna tace. “Hajiya ga Kakar Khausar”. Murmushi Hajiya Bunayya tayi Idanunta akan Khausar tace. “Ai na ganeta Hajja Nana sannu da zuwa ina yini ya gajiya kunzo lafiya?”. Ita kuwa Amina batare data ƙarasa shiga falon ba ta ɗaga sautin Muryanta da faɗin. “Khausar!, Khausar!! Khausar!!!,”. Daga ciki Khausar tace. “Me?". Afusace Amina tace. “Bana son rashin kunya ni zaki yiwa rashin kunya? ina kiranki kina jina ba zaki fito ba aikin san dai tunda na kira ki ina da ɓuƙatar ki!”. Jin surutan da take yasa Khausar ta fito tare da tsayawa daga bakin ƙofa ta riƙe ƙugunta kana tace. “To ai tunda ke kike da ɓuƙatata kinsan inda dakina yake sai ki shiga ki sameni”. Cike da kirsa Hajiya Bunayya tayi dariya tana kallon Khausar tace. “Kudai in Kun hadu bakwa rabuwa da faɗa kamar wasu ƙananun yara Allah dai ya kawo muku sauƙi kuna na kamar wuta da Auduga”. Juyawa Hajja Nana tayi ta kalli Khausar da Amina kana ta taɓe baki tare da cewa. “To ai kinsan haka al'amarin yake, mu zuriyarmu bama gani mu ƙyale sannan bama ji muyi shiru, sannan su kuma mayu haka suke basason mai baki shiyasa baza'ayi shiri ba”. Hajiya Bunayya tayi saurin cewa. “Hmmm Hajiya ai tsatsonne na mayu su basu tsotsaba dan mu atsarkake muke”. Kallon mamaki Mommy tayi mata kana tace. “Hajiya har ke kin yarda da kalmar kenan?”. Hajiya Bunayya ta taɓe baki kana tace. “Ha'a abinda ake faɗa musu acikin gari mun isa mu hana ne?”. Atake fara'ar dake fuskar Mommy ya gushe cikin rashin jin daɗin abinda Hajiya Bunayya ta faɗa tace. “Wallahi sukam ba Mayu bane har dake ki yarda kefa komin yaya, ita Uwa ce agareki kuma kakar ’ya'yanki kuma Inde har za'ace suna ciki to mijinki ma yana ciki”. Hajiya Bunayya kuwa cikin sauri tace. “A'a mijina atsarkake yake. Uwarsa kuwa ba zan musan ta mata ba yawwa a duniya idan kaji an cewa mutum maye ba zaka musanta masa ba kawai dai abinda na sani mijina ba yayi nima banayi kuma 'ya'yana na basayi. Hajja Nana gaskiya kika faɗa taje can ta ƙarata da baƙin halinta inma tanayi can mata inma ba tayi can mata amma abinda gari dai ake faɗa tana yi, kuma mutum bashida hujjar da zaiyi musu akan hakan, gwara ma hujjar da mutum zai ɗabbaga tunda ga alamu ke yanzu ko cikin ki dake yawa zubewa bakya ta Allah ƙashi da ita!?”. Cikin sauri tare da ɗaure fuska Mommy tace. “A'a nikam Allah ne ya ƙaddara min zubewar ciki babu wani wanda ya zubar min da ciki”. Murmushi Hajiya Bunayya tayi aƙasan ranta tace can miki ƙidahuma. Khausar kuwa kallon mamaki tabi Hajiya Bunayya dashi kana aƙasan ranta tace lalle Hausawa sunyi gaskiya da suka ce iya ruwa fidda kai”. Amina dake tsaye ta watsa Khausar Harara kana tace. “Abbah ke kiranki kizo kakar taki tazo da wasu maza suna waje sai kije ku gaisa”. Ta ida maganar tare da juyawa ta fice. Ita kuwa khausar cike da farin ciki ta juya ta fice ta nufi coumpund kasa ɓoye fara'ar fuskarta tayi ganin Yaya Aliyu tsaye yaron Baffanta na Adamawa tare da Yaya Abba cikin jin dadi ta ware manyan Idanunta cike da farin ciki tace. “Yaya Aliyu sannu da zuwa ku ƙara so”. Ta faɗa tana yin gaba zuwa Falon Lamiɗo dake saukan baki. Bayan sun shiga falon sun zauna ta dubi Aliyu still Fuskarta da murmushi tace. “Yaya Aliyu yaushe kazo?". Gyara zamansa yayi yana fuskantar ta kana fuskarsa ɗauke da murmushi yace. “Baffanki ne ya tasoni wai sai na kawowa tsohuwar sa kayan azumi shine kuma yanzu Hajja Nana tace sai munzo”. Khausar kuwa murmushi tayi kana tace. “Hajja Nana rigima" Sai kuma ta maida kallonta kan Yaya Abba dake latsa waya tace. “Yaya Abba ya karatu?”. Ahankali ya ɗago kansa da murmushi afuskarsa yace. “Karatu ya ƙare yanzu wannan karon tare zamu tafi da Aliyu can Adamawa idan Allah ya nufa idan munje zan samu aiki Insha Allah tunda kinga Baffan Jimeta yana da hanya da manyan mutane Insha Allah za'a samu”. aSaki murmushi tayi kana tace. “Masha Allah abu yayi kyau”. Lamiɗo ya shigo suka gaisa bayan sun gama gaisawa ya fita, Khausar kuwa Anutse ta miƙe tace. “Ina zuwa”. sannan ta fice. Kai tsaye kichen ɗin su ta nufa ta ɗauko Babban Warmers da faranti ta fita. Hajja Nana ta bita da kallo baki sake ganin Uban kula me kyau da tsari da tafita dashi. Ba daɗewa Khausar ta dawo ta sake ɗaukan Flaks da kofuna. Har takai ƙofa Hajja Nana data kasa haƙuri tace. “Kede akwai Jaira mara kirki tunda nazo kike wani shan ƙamshi kamar baki so zuwa na ba, ko arzikin gaisuwa ban samu ba bare insa rai da ruwan sha, amma wa'annan saboda 'yan uwanki ne jiki na rawa kin wani kinkimi Uban kula kin fita yanzu kin dawo kin ɗauki Flaks”. Kallonta Khausar tayi tare da taɓe baki tace. “Kinga sai anjima Ni sauri nake”. Tana gama fadar haka ta fice bakinta ɗauke da Sallama tashiga falon. Amsawa sukayi tare da kallonta. Zama tayi tare da buɗe Warmers din ta ɗauki babban Plate ta zuba musu shin kafa da miyar da yaji naman kaza sai kuma haɗin coslow kana ta zuba musu shayi dake tururi. Yaya Abba yayi Murmushi yace. “Da'alama wannan girkin kine saboda wannan ƙamshi”. Murmushi tayi amma batace Komai ba. Acan ɗaki kuwa bayan ankira sallan Azahar Mommy takai Hajja Nana har toilet ɗin ta tayi alwala kana ta fito ta gabatar da Sallah bayan ta idar tayi adduo'i. Ta juya ta kalli Mommy dake riƙe da carbi ahannunta tace. “Aisha”. Cike da girmamawa Mommy tayi ƙasa da kanta kana tace. “Na'am” Hajja Nana kuwa gyara zamanta tayi tare da tattara duk kan nutsuwarta zuwa kan Mommy tare da cewa. “Magana ce mai muhimmanci ta kawoni”. Cikin girmamawa Mommy da kanta ke ƙasa tace. “Toh ina sauraronki Hajja Nana”. Hajja Nana kuwa Ajiyar zuciya ta sauƙe kana tace. “Magana ce akan Khausar da kuma ɗan Baffanta wato Aliyu”. Jinjina kai Mommy tayi cike da ladabi tace. “Toh Hajja Nana ina jinki”. Hajja Nana ta gyara zamanta tare da cewa. “Toh zuwa yanzu dai inaga Khausar ta girma, sannan inaga ta gama karatun ta yanzu idan ma bata gama ba to ta kusa”. Jinjina kai Mommy tayi kana tace. “Eh ta kusa Insha Allah yanzu kam Shekara ɗaya yarage bayan sallah Insha Allah zata tafi ajin ƙarshe na gama makarantar gaba da primary”. Cikin jinjina kai Hajja Nana tace. “Masha Allah Ubangiji ya taimaka”. Mommy ta amsa da. “Ameen ya hayyu ya ƙayyum”. Hajja Nana kuwa duk kan nutsuwarta ta tattara tare da cewa. “To ai yanzu dai ta samu ta kori jahilci ta yaƙesa, yanzu batun aurenta za'ayi. Ga kuma Yayanta kuma ɗan Uwanta za'a aura Matashi magana ya ƙare sannan kuma idan karatun take so ta cigaba idan sunyi aure zata yi acan jahar Adamawa tunda suna da makarantu manya-manya acan dan haka yanzu batun aure ne ya kawo mu nazo dashi za'a haɗa bayan sallah in Allah ya yarda”. Akuma dai-dai lokacin Khausar ta shigo ɗakin, cike ka ɗuwa Idanunta na kan Hajja Nana cikin sauri tace. “Wai me naji kina cewa?”. Cikin isa, gadara, Hajja Nana ta wurga mata Harara kana tace. “Batun Aurenki nakeyi”. Arazane Khausar ta zare ido kana tace. “Wa.....! *GARKUWAR* taku ce dai MA'AURATA, da masu shirin aure, da masu jego, da yan gayu masu son k’amshi kece raini, da gyaran da zaike maimaita muku dararen forkon kuruciya* Ko kunsan Jikinmu na da sinadaran hormones da suke taimakawa dan’adam akan komai musamman lokacin da mace take mu’amalar aure da mijinta. Mafi akasari wannan hormones din ne ke samun matsala ko su yi sanyi koma su daina aiki kwata-kwata shi ne dalilin da zai sa mace tace bata jin sha’awa ko bata san dadin aure ba. Albishirinku ina da kayan da ke taimakawa wannan sinadaran du dawo aiki tukuru don karkato miki da kimarki wajan mai gida sannan su taimakawa wannan sinadaran hormones dinki su dinka secreting din ni’ima wadatacciya da zata taimaka miki ki gamsu mijinki ya gamsu fiye da tunaninki. Note: Kayana ba sa tsinka ruwan ni’ima suna dai taimakawa hormones dinki ne su tsattsafo da ni’imar musamman wacca cutar sanyi ko dattin mahaifa ya dankarar da su ya hana su yin aikinsu yanda ya kamata. Haka zalika idan kina da kyau ki kara da wanka. Zaki iya amfani da magani na na gargajiya wanda zai gyara miki sex hormones din kullum ki kasance cikin humidify wato cikin damshi mai albarka kamar yanda ake son mace. Yana gyara miki mara. Sai kamshi. Hajiyata daure ki fara amfani da turarena ki ji irin salon kamshin sa salo ne da zai daidaita ki da mijinki ya kankaro miki da kimarki a wajansa. Siyan na gari mayar da kudi gida. Ga masu buƙata ga number' wayata wanda nake whatsApp dashi 09097853276 kimin mgn ta whatsApp in har kin tabbatar kin shirya saya mu dai-dai ta, kayana ba ƙanana bane, shiyasa bana harkan karanta, muddin kinsan baki shirya sayaba Please kada kiyi min mgn ki bari sai kin shirya kuɗinki a hannu, ba ina nufin kayana bana talaka bane, no akwai ƙananan set na masu karamin karfi, banson aimin mgn a ɓatamin lokacin aiyukana a shirme baki shiryaba. Shine karantan da bana so. 0005388578 Jaiz bank AISHA GARKUWA ALIYU. In kin shirya ga number ta ga kuma account number ta wanda in mun gama mgn zaki turo kudin ki, kana insa miki kaya a mota, duk ƙasar da kike kayana zaije gareki, amman fa in kinada dalilin zuwan nasune🤝🏻sayan na gari meda kudi gida. GARKUWAR MA'AURATA By *GARKUWAR MARUBUTA* 📝✨💫⏰🤴🏻👹❤️❤️❤️🍇 *SAKAYYAH* _Page 13_ _NA_ *AYSHA ALIYU GARKUWA* 🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 Littafin SAKAYYAH na kuɗine ƴar uwa ki biya ki karanta cikin Aminci da salama, ba haƙƙin kowa akanki. Littafin 1k ne kacal 0661110170 GTBank AISHA ALIYU GARKUWA sai ki turo min shaidar biyanki ta WHATSAPP 09097853276. Sai in saki a Group ɗin littafin inda zan rinƙa posting. *WOHOHO IN KAJI ANA ƘI GUDU TABBAS SA GUDU NE BEZO BA* _Ina kuke Ma'aurata masu sha'awar ganin sun zama taurari kuma fitilu a idanun mazajensu Uwar gida,Amarya,Tsakar gida,hadda tan kaɗen gida Shararriya kuma ƙasaitacciya data saba kawo muku nau'ikan sirrin sahihan magungunan ma'aurata wato *AYSHA ALIYU GARKUWA* Garkuwar Marubuta ayau ma ta dawo muku da Ingantattun magungunan mata masu kyau da inganci domin gyara kanki ki zamto tauraruwa a idanun mijinki...Muna da Ingantattun Abubuwa kamar haka_ :_Munada Garin mallaka, garin maɗi, garin Hakkin mayi, garin ɓelɗamhi Garin ilanwaddihi, Gumbar da ba'a baiwa mai kishiya, Gumbar kolli mai kellin al'khairi, Gumbar Riɗi wato 3 in 1, Gumbar makwaranyi, Masin Maliƙi mai masifar ƙarfi da matse mace, ka masin Daɗi har Maɗigan Akwai, kwanon ƙasaitacciyar mace mai masifar kyau da ratsa jiki da samar da inƙantacciyar ni'ima yanada abubuwa masu kyau haɗinsa, Zumar goron tula mai masifar kyau, tsumin dabino, mai ratsa jiki, tsumin Riɗi mai ƙarfi, Furar Mata mai tsastsafo da ni'imantaccen damshi, Cida kaza, Ciccibi Abodi, Tsumin Ɓaure, tuwon ɓauren, kana akwai maganin sanyi sadidan, da dai sauransu...Se kuma fannin ƙamshi kasance da Shu'umin ƙamshi wanda ze gigita ƙwaƙwalwar Oga tare da jin ko wacce mace bata kaiba...._ _Shin ko kina da labarin Miskilinci da ƙasaitar Rayyan Naaan amma lokaci ɗaya ya zamto zautacce sakali akan soyayyar Jannart bakomai Jannart ta riƙe ba face sirrinkan gyara da kuma shu'uman humran da kulaccar sirri na Aysha Aliyu Garkuwa(Tubali) tabbas taga tasirin haka domin Naanunta ya zame mata tamkar bawa_ _Shin ko kinsan sihirtaccen haɗin da Aysha ke sha kenan ta zamto tauraruwa a idanun Hamma Yusuf(Miwasmiti)...Tabbas Mahmud ya zamto zautacce kuma makaho akan sauyayyar Bazawara wato khadijarsa duk da kuwa gashi da budurwa(Namiji Baya Kaɗan) ko kinsan hakan nada alaƙa da amfani da sahihan maganin da kuma shu'uman humran Aysha Aliyu Garkuwa??.Nasan ba zaka ku manta da irin kima da kuma darajar da Aysha ke dashi acikin Idanun Sheik Jabeer ɗin ta duk da kuwa shekaru sunja anma jinta yake tamkar budurwa 'yar sha bakwai(Garkuwa) sirrin hakan na tare da Ingantattun kuma sahihan magungunan Aysha Aliyu Garkuwa Wato Garkuwar Marubuta da kuma Ma'aurata na tabbata kunsan da cewa basirarta ba'a iya rubutun littafi ya tsaya ba hadda inganta rayuwar ma'aurata ta hanyar kawo musu Nagartattun abubuwa Ga duk wacce ta shirya saya seta tuntuɓi number ta 09097853276 muna iya tura kayan mu aduk inda kuke afaɗin Nigeria harma da ƙetare Dan Allah 'yar uwa idan baki shirya siyaba kada kiyi min magana muɓatawa kanmu lokaci...._ 🤝🏻🤝🏻🤝🏻🤝🏻🥰😘sai.kunzo. sayan na gari maida kuɗi gida, Khausar kuwa cikin tsare Hajja Nana da ido ta riƙe ƙugu tare da cewa. “Gaskiya nikam bana son irin wannan mulkin mallakar naki”. Da sauri Mommy ta ɗaga mata hannu fuskarta babu walwala ta kalli Khausar kana tace. “Kifita, daga nan Khausar!”. Lokaci daya fara'ar data shigo da shi ya gushe ɓacin rai ya mamaye mata zuciya juyawa tayi ta fice daga Bedroom ɗin Mommy ta nufi nata tana shiga Bedroom ɗin ta jiyo Muryan Asma'u afalo. Kai tsaye Bedroom ɗin Khausar Asma'u ta shiga tare da cewa. “Assalamu Alaikum”. Atare Dije da Khausar suka amsa da. “Wa'alaikum Salam”. Asma'u naganin fuskar Khausar ta ware Ido kana tace. “Ya dai mutuniyar naga fuskarki haka?”. Wani abu mai masifar ɗaci Khausar ta haɗiye Idanunta akan Asma'u dake tsaye ta gyara zamanta tare da faɗin. “Babu komai ƙara so ki zauna”. Zama Asma'u tayi tare da tsare Khausar da ido ganin yanayin damuwa atare da ita. Kallon Dije Khausar tayi sai kuma ta juya ta kalli Asma'u tare da faɗin. “Wannan Itace Dije”. Murmushi Asma'u tayi Idanunta akan Dije ta ajiye Handbag din dake hannunta kana tace. “Sannunki”. Murmushi Dije tayi tare da faɗin. “Yawwa”. Juyawa Asma'u tayi tare da kallon Khausar kana tace. “Khausar wacece ban ganeta ba”. Muskutawa Khausar tayi tare da gyara zamanta kana tace. “Dije ce wacce nake baki labarin ta a Jauro Yaya”. Jinjina kai Asma'u tayi tare da faɗin. “Ohh Ayyah na tuna ta itace tazo ita da Hajja Nana suka zone?”. Khausar kuwa kai ta gyaɗa mata kana tace. “Eh" Murmushi tayi tare da faɗin. “Ai lallai dai kam kice muna da manyan baƙi Dije amma zamu daɗe ko?”. Kai ta girgiza tare da yin murmushi kana tace. “A'a yau zamu koma ”. Ware ido Asma'u tayi tare da faɗin. “A'a yau zaku koma kuma?”. Sai kuma Asma'u ta juya ta kalli Dije kana tace. “Shaf-shaf haka?”. Ita dai Khausar na gefe ta jingina bayanta da jikin gado Idanunta alumshe tana tunanin maganar Hajja Nana. Kai Dije ta gyaɗa tare da faɗin. “Eh ai da Yaya Aliyu muka zo”. Murmushi Asma'u tayi kana tace. “Ayyah ai kam munji daɗin ganinki”. Asma'u kuwa juyawa tayi tare da kallon Khausar wacce ta tsirawa waje ɗaya Idanu cike da kulawa Asma'u ta dafa kafaɗar ta kana tace. “Wai Meye ne kike ta haɗa rai!?”. Iska mai zafi ta furzar tare da kallon Asma'u fuskarta babu walwala ta saki Ajiyar zuciya kana tace. “Kina ji wata magana da wannan tsohuwar tazo dashi wai batun Aurena!kuji min tsohuwar nan da wani iyayi ta bari Iyayena suyi magana akai na mana ita kuma kaka wake maganarta!?”. Asma'u kuwa Dariya mai sauti tayi tare da cewa. “Iyeeee kice zamu sha bidiri!”. Dije tayi murmushi kana tace. “Barta dai kuma ma kinga mijin data samun ne kyakkyawa fa?”. Baki Khausar ta kuma taɓewa tare da wurga musu Harara kana tace. “Toni ina ruwana dashi?, Ni bana so kada ma ayimin wannan maganar tsakani da Allah shi yafara Auren yayata fa Asma'u”. Da sauri Asma'u ta ɗago kanta tare da cewa. “Addarki kuma?, Dama ba kece ƴar farin Mommy ba?”. Jinjina mata kai Dije tayi tare da cewa. “Eh ba ita bace ƴar fari Akwai Addarta Nenne Amma ta rasu kuma itama Yayanta Aliyu aka aura mata sunyi aure da shekara biyu ta samu ciki tazo wajen haihuwa ta rasu!”. Asma'u ta jinjina kai tare da cewa. “Allah sarki Allah ya gafarta mata,. Ohh Ashe shiyasa Mommy bata kunyar kiran sunanki nida duk atunanina kece ƴar fari har nace Mommy ƴar zamani ce bata ɓoye sunan ki”. Kai Khausar ta girgiza kana tace. “A'a ba nice ƴar fari ba ni ta biyu ce”. Murmushi Asma'u tayi tare da faɗin. “Ohhh lalle kam kice zamu sha biki”. Khausar kuwa fuska ta tsuke kana tace. “Zaku sha bikin waye?”. Dariya Asma'u tayi tare da cewa. “Bikin ki mana”. Cikin haɗe rai Khausar kai ta girgiza tare da faɗin. “Asma'u kiyi min fatan alkhairi mana, kina jin tsohuwar nan da shiririta da shirme wai ko bayan sallah za ayi ko menene oho?”. Dije kam kai ta girgiza tare da cewa. “Bafa cewa tayi bayan sallah ba ita dai alissafinta ki gama karatunki sai anyi idan yaso in kinaso kici gaba da karatunki sai Yaya Ali ya saki ki cigaba dayi a Adamawa bayan sallan baɗi take nufi”. Fuska Khausar ta ya mutse kana tace. “Aima Allah ya kiyaye abar mutum yayi karatunsa mai zurfi mana sannan ai mutum nada tsarin rayuwarsu da kuma yanda yake so ya kasance haka kawai sai atakura min”. Dariya Asma'u tayi tare da cewa. “Mu dai kar ki mana baƙin ciki ki hana mu shan biki”. Harara Khausar ta maka mata kana tace. “Ai sai kuyi shagalin ku kuka ɗai”. Dije na dariya ta dubi Khausar kana tace. “Yo ina zamuyi shagali ba Amarya ai dan ke za'ayi”. Baki Khausar ta taɓe kana tace. “Ai lalle dai kam”. Mommy ce tashiga ɗakin bakinta ɗauke da sallama kallon Asma'u tayi kana tace. “A'a Asma'u kece yaushe kika zo”. Asma'u kuwa zamewa tayi daga kan gadon tare da cewa. “Ban daɗe da zuwa ba Mommy Ina yini?”. Mommy ta amsa da. “Lafiya lau alhamdulillah yasu Umminki?”. Miƙewa Asma'u tayi tare da zama agefen gadon kana tace. “Tace agaisheki”. Masha Allah Mommy ta faɗa tare da maida kallonta kan Dije kana tace. “Dije kizo Hajja Nana na kiranki wai zaki rakata gidan Aminiyarta”. Ta ida maganar tare da juyawa ta fice. Miƙewa Dije tayi tare da kallon Khausar kana tace. “Khausar mu tafi mana”. Fuska Khausar taya mutse kana tace. “A'a kuje kawai Allah ya kiyaye hanya ni bazan jeba, muyita faɗa da ita a gidan mutane muna raba hali agidan mutane duk inda mukaje sai ansan mu”. Murmushi Dije tayi tare da faɗin. “Toh shikenan mun tafi”. Sannan ta fice kai tsaye ɗakin Mommy ta wuce sannan ta samu Hajja Nana atsaye. Hajja Nana na kallonta tace. “Wuce ki kira su Aliyu mu tafi”. Kai Dije ta gyaɗa sannan ta fice. Mommy kuwa Jakar data haɗa wa Hajja Nana tsaraba ta ɗauka sannan ta fice. A coumpund ɗin ta samu Yaya Aliyu da Yaya Abba tsaye jikin mota cike da girmamawa da kuma ladabi Ya Aliyu ya kalli Mommy tare da cewa. “Toh Mommy mun gode Allah ya saka da alkhairi Allah yabar zumunci”. Murmushi Mommy tayi tare da cewa. “Amin, Allah ya tsare muku hanya”. Hajja Nana ta amsa da. “Ameen”. Tare da buɗe bayan motar tashiga Dije ta zauna agefenta Yaya Aliyu na gefen mai zaman banza Yah Abba kuwa shike Driving suka fice daga gidan. Sai da Mommy taga fitar su sannan ta koma cikin gida. Yaya Abba kuwa kai tsaye gidan su Moddibo ya nufa. Hajja Nana nayi masa kwatance har suka isa gida suna shiga gidan. Cikin sauri Yaya Ali ya lumshe Idanunsa kana yace. “Masha Allah wlh Ina son garin Gembulan nan saboda yana da kyawun tsari dan yafi Adamawa kyawun tsari da komai akwai yanayin sanyi da daɗi”. Jinjina kai Yaya Abba yayi yace. “Aikam sosai ma”. Yaya Ali ya juya tare da kallon Hajja Nana kana yace. “Hajja Nana wannan kuma gidan wacece ɗinkin ne?”. Murmushi Hajja Nana tayi alokacin da take sauƙa amotar ta kalli Ali kana tace. “Ƙawata ce tare mukaje da ita aikin hajji na farko na biyu ma tare muka je sannan ko daga baya muna yawan zuwa Umarah tare da ita”. Murmushi Yaya Ali yayi tare da cewa. “Ai dai lalle kam kice gidan Aminiyar kice?”. Dariya Hajja Nana tayi tare da cewa. “A'a sosai ma kam”. Dai-dai lokacin da suka isa ƙaramin gate ɗin da zai sadaka da farfajiyar tsakar gidan Innayi. Innayi dake zaune ta hango Hajja Nana da baƙi abayanta, Cike da fara'a ta miƙe da sauri fuskarta ɗauke da ƙayataccen murmushi mai cike da jin daɗi ta matso kusa da Hajja Nana kana tace. “Aaaa Lalle marhaba Hajjaju Makkatun Masha Allah Hajiya Nana mutanen Makka lale marhaba ku iso”. Ta faɗa tare da juyawa ta shiga ɗaki tare da ɗaukan lallausan Chanis capet ta shimfiɗa musu. Sai kuma ta fito cike da farin cikin daya kasa ɓoyuwa afuskarta kallon Yaya Ali tayi tare da cewa. “Wannan shine Mijin namu na Adamawa da kike bamu labarin?”. Kai Hajja Nana ta gyaɗa tana murmushi kana tace. “Eh”. Innayi ta juya ta kalli Hajja Nana kana tace. “Ku shiga”. Sannan ta kalli Yaya Abba da Yaya Ali kana tace. “Ku ƙara so”. Ta faɗa tare da ficewa Innayi ta nufi sashen Moddibo tare da cewa. “Moddibo, Moddibo ga baƙi munyi” Shi kuwa Moddibo atare suka miƙe da M Jameel suka fito. Ɗan sake fuska Moddibo yayi kana yace. “Sannunku da zuwa ku iso”. ya faɗa tare da matsa musu. M Jameel na ganin Yaya Abba ya miƙa masa hannu fuskarsa ɗauke da murmushi kana yace. “Ha'a Abba kaine?”. Murmushi Yaya Abba yayi kana yace. “Ni ne dai”. M Jameel yayi dariya kana yace. “Sannu ku da zuwa”. Yaya Abba na bin bayansu yace. “Laaa Jameel nan gidan kune?”. M Jameel yayi Murmushi tare da shafa sajensa ya kalli Yaya Abba tare da faɗin. “Eh gidan mune!” Murmushi Yaya Abba yayi da faɗin. “Masha Allah”. sannan suka shiga falon din wanda tuni Ya Ali da Moddibo suka shiga. Innayi dake tsaye ta juya tare da cewa. “Moddibo zoka kawo musu abin taɓa wa”. Daga ciki Moddibo ya miƙe kana yace. “Toh Innayi”. Sannan ya fice tare da bin bayanta. Juyawa Innayi tayi tare da kallon Moddibo dake biye da ita kana tace. “Kashiga daga ciki ka gaida ƙawata Hajja Nana dana ke ce maka munje aikin Hajji na farko dana biyu kuma yawanci Umarah ma tare muke zuwa ɗakin mu ɗaya tun da take zuwa gidan nan bata taɓa samunkaba, Kai ya gyaɗa da faɗin. “Na'am”.Ya ida maganar tare da shiga ɗakin bakinsa ɗauke da sallama Idanunsa ya sauƙa akan tsohuwar da yaje ya yamata ta'aziyya a Jauro Yaya. Cike da nutsuwa da kuma ladabi ya zauna daga gefenta kana yasa hannu ya shafa sajensa cikin yanayin rashin walwalarsa yayi ƙasa da kansa tare da cewa. “Sannun da zuwa”,Ya gaisheta batare daya nuna ya ganeta ba. Hajja Nana kuwa Kallonsa tayi kana tace. “A'a kamar nasan wannan fuskarta fa, kwanaki kamar kunje da wani abokin Malam Liman mai suna Malam Arɗo ko?”. Kai Moddibo ya jinjina still Kansa a ƙasa kana yace. “Eh”. Murmushi Hajja Nana tayi kana tace. “Ayyah sannun ka ashe dai Jikana ne Allah yayiwa rayuwarka albarka Allah yabaka zuri'a ɗayyiban”. Still Kansa A ƙasa ya shafa kwantaccen sumar kansa mai sheƙi da yalƙi kana yace. “Ameen Ngd”. Ya ida maganar a taƙaice tare da miƙewa ya fice. Tiren da Innayi ta haɗa Gasassun Zabbi da M jameel yasa ta gasa musu, shinkafa da miyar dage-dage da yaji naman kaza sai Akwashi dake ɗauke da ƴaƴan itatuwa ta miƙawa Moddibo amsa yayi kana ya nufi sashen sa dashi. Bakinsa ɗauke da Sallama yashiga tare da ajiye Tiren akan center table dake tsakiyar falon kana ya maida kallonsa kan M Jameel dake ta hiran Yaushe gamo da Yaya Abba kai ya girgiza tare da cewa. “J miƙo musu ruwa acikin fridge ka barsu haka gashi har na dawo baka kawo musu komai ba”. Murmushi M Jameel yayi kana yace. “Wallahi muna ta hiran yaushe gamo da Abba nasan sa mun taɓa haɗuwa dashi a Adamawa”. Jinjina kai Moddibo yayi tare da jingina bayansa da jikin kushin kana ya lumshe idanunsa tare da cewa. “Ayyah ashe kunsan juna”. Kai Yaya Abba ya gyaɗa alamar Eh. Ya Ali kuwa hankalin sa ya mayar kan wayarsa yana latsawa. Acan ɗakin Innayi kuwa zama Innayi tayu tare da kallon Hajja Nana kana tace. “Yanzu ma kinzo wajen jikar tamu ce?”. Kai Hajja Nana ta gyaɗa kana tace. “Eh wallahi". Murmushi Innayi tayi tare da cewa. “Shine baki zomin da ita ba”. Baki Hajja Nana ta taɓe tare da faɗin. “Barta ba shiri muke da ita ba fitsararriya ce yanzu ma nazo ne akan batun aurenta da yayan ta amma na lura ma kamar batason abin ko yayane ohon mata kinsan ƴaƴan yanzu da tsaurin ido su suke zaɓawa kansu maza yanzu ma na barta tana can tana kumbure kumburen baki”. Murmushi Dije da ke kurɓan tes tayi aranta tace Dramer Hajja Nana da Khausar bai ƙarewa. Innayi kuwa murmushi tayi kana tace. “Ayyah ai da tazo na ganta kice mu shirya akwai shan biki?”. Dariya Hajja Nana tayi kana tace. “Ai dai kam Insha Allah akwai shan biki dan biki yana nan yana tafe”. Innayi kuwa kai ta gyaɗa kana tace. “Lallai abu yayi kyau amma dai zamu kwana”. Girgiza kai Hajja Nana tayi kana tace. “A'a yanzu ma zamu tafi dan mun sallami can kam da zan tafi da jikar tawa ma to sai mahaifiyata take ce min bata da lafiya don haka na barta saboda tana taimakawa mahaifiyar tan da ɗan aikace-aikacen yau da kullum”. Kai Innayi ta jinjina tare da faɗin. “Ayyah Allah yabata lafiya. Yaushe zamu koma Umarah bana zaki je na Ramadan?”. Hajja Nana kuwa kai ta jinjina kana tace. “Eh Insha Allahu zanje in Allah ya yarda amman ta Adamawa zan tashi kefa zakije kuwa?”. Murmushi Innayi tayi tare da cewa. “Nima zanje in Allah ya yarda amman kin san ni ta nan Jaligo zan tashi”. Kai Hajja Nana ta gyaɗa tare da faɗin. “Abu yayi kyau Ubangiji Allah yasanya alkhairi Allah ya bamu sa'a”. Innayi ta amsa da. “Ameen”,kana ta cigaba da cewa. “Nima zamu tafi da jikina da kuma abokinsa tare za muje”. Dariya Hajja Nana tayi kana tace. “A'a abu yayi kyau to sai mun haɗu acan ɗin”. Hiran yaushe gamu suka cigaba dayi yayin da Dije ke gefe tana yagar Gashesh-shen Zabbi da nonon shanu mai ɗumi. Acan falon Moddibo kuwa bayan sun gama gaisawa Yaya Abba da Yaya Ali suka sha fruit din kana suka ci gashshen Naman dake fitar da ƙamshi tare da ruwan Tea mai zafi. M Jameel ya kalli Yaya Abba daya koma ya zauna tare da rufe Warmers din Cike da kulawa ya sake Kallonsa kana yace. “Abba ya bakuci abincin ba”. Murmushi Yaya Abba yayi kana yace. “Wallahi aƙoshe muke yanzu ma dan kar kuce munƙi cin komai ne amma Alhamdulillah”. Murmushi M Jameel yayi kana yace. “Toh shikenan”. Miƙewa sukayi Atare jin Innayi na cewa. “Moddibo kufita Hajja Nana zasu wuce”. Da to Moddibo ya amsa kana suka fita cike da kulawa M Jameel da Moddibo suka kalli yaya Abba da yaya Ali atare suka haɗa baki wajen faɗin. “Toh mun gode da ziyara Allah yabar zumunci”. Yaya Ali ya amsa da. “Ameen”. Sannan Yaya Abba yashiga mazaunin Driver Yaya Ali kuma ya zauna gefen mai zaman Banza yayin da Hajja Nana da Dije suka zauna abaya M Jameel ya miƙa kansa ta window tare da ajiye wa Hajja Nana kuɗi akan cinyarta tare da cewa. “Allah ya tsare”. Murmushi tayi kana tace. “Allah ya muku albarka nagode”. Motar Yaya Abba yaja suka fice saida motar ta fita layinsu kafin Innayi, Moddibo,da kuma M Jameel suka koma cikin gida. Cikin awa biyu Hajja Nana suka isa Jauro Yaya Washe gari Da safe yaya Ali ya koma Adamawa dashi da Abba suka tafi. A ɓangaren Khausar kuwa tunda daga ranan da Hajja Nana tayi mata maganar aure ta watsar da maganar kasancewar Momynta bata sake yi mata maganar ba ita ma bata sake tada maganar ba hakan yasa bata ɗauki maganar da muhimmanci ba ita kuwa Mommy tasa aranta tun daga Ramadan ya kawo kai ta samu dama ta yanda zata roƙowa ƴar ta al'khairi idan har Aliyu al'khairi ne agareta Allah ya tabbatar mata da al'khairi idan kuma ba al'khairi bane Allah ya zaɓa mata mafi al'khairi shima kuma Allah ya musanya masa da mafi al'khairi. Yau ya rage azumi saura kwana biyu da hantsi Mommy na zaune afalo taji Sallamar sabon mai gadinsu da aka kawo kallon Khausar dake riƙe da hisnul Muslim tana Azkhar tayi sai kuma ta maida kallonta ga Haiydar dake danna wayarta ta gyara zamanta tare da cewa. “Haidar jeka duba lafiya Namadi ke Sallama”. Kai Haiydar ya gyaɗa kana yace. “Toh Mommy”. Sannan ya miƙe ya fita. Kallon Namadi dake tsaye yayi kana yace. “Lafiya kuwa”. Kai Namadi ya gyaɗa tare da faɗin. “Kayane Alhaji ya aiko dasu Azo ashiga dashi ciki”. “Ok kashigo dasu”. Ya faɗa tare da juyawa ya koma ciki. Kallon Mommy Haiydar yayi kana yace. “Kayan azumine Abbah ya aiko dasu shine Namadi zai shigo dasu”. Jinjina kai Mommy tayi tare da cewa. “Ok”. Da Sallama Namadi yashigo kansa ɗauke da buhun shin kafa ya ajiye a store kana ya koma ya ɗauko na ɗanyen shinka yakai, sannan ya kuma kimawa ya rinƙa shigo da catton ɗin indomie, Catoon ɗin Spaghetti, Cotton ɗin Macoroni, Couscous, Buhun fulawa, Buhun niƙeƙƙen garin gero na kunu, buhun wake, buhun sugar Corn Flakes, Madara, Patoto, Doya Crate din ƙwoyi Jarkan mai Jarkan man ja haka ya riƙa shigowa da tarkacen kayan buƙata na Ramadan. Kamar yanda ya kawo sashen su Khausar haka ya kai sashen Hajiya Bunayya. Yayinda hakan take a kowani gida haka magidanta suka riƙa shiga da kayan azumi domin shiryawa wannan wata mai falala. Acan ɓangaren gidansu Moddibo kuwa shida M Jameel amota Moddibo ke driving yayin da M Jameel ke gefen mai zaman banza sai kuma wani yaro daga baya mai suna Iro wanda ke musu aika hong sukayi aƙofar gidansu Moddibo kana suka shiga cikin gidan bayan Iro ya fita ya buɗe musu. Innayi na zaune atsakar gida akan kujera ƴar tsugunno taji ƙaran mota na shiga cikin harabar gidan aranta tace yau lafiya Moddibo ke shigowa da mota har cikin gidan. Moddibo kuwa kusa da Innayi yayi Parking motar tare da buɗe Murfin motar ya zira ƙafarsa ɗaya awaje ɗaya kuma na ciki M Jameel da Sadik kuma suka fita kusa da Innayi M Jameel ya zauna shi kuwa Sadik Boot ɗin motar ya buɗe tare da fito da buhun far n gero, Buhun wake, Buhun shinkafa ɗanye da gumi, Catoon ɗin indomie, Catoon, Spaghetti, Bushesh-shen kifi crate ɗin ƙwoyi, Gongwanaye mayen madara da Vournvita buhun, Sugar kwalin Lipton sai kuma naman rago da aka gyara gaba ɗaya ga kuma na shanu ga kifaye duk Sadik yasa su a fridge Kallon Moddibo Innayi tayi sai kuma ta maida kallonta kan M Jameel dake kusa da ita tayi tare da cewa. “Lalle kayan Azumi sun saƙƙo ga Azumi sai ƙaratowa yake yau saura kwana biyu ko uku”. Kai M Jameel ya gyaɗa kana yace. “Ai dai kam Innayi azumi yazo”. Ya ida maganar tare dasa hannu acikin aljihunsa ya ciro Bandir ɗin kuɗi kimanin dubu ɗari ya miƙawa Innayi tare da faɗin. “Innayi gashi babu yanda banyi da Moddibo ba yabarni in saya miki kayan Azumi amma dake ɗan baƙin haline baya so in samu lada yaƙi furrr yace komai shi zai siya gashi wannan ki riƙe kiyi yadda kika ga dama dasu”. Kallon kuɗin Innayi tare da Girgiza kai kana tace. “Ayyah Jameel am bana son wannan shungullan yanzu ni kuma me zanyi da wannan kuɗin kabar su Jameel am ni ba ɓuƙatar su nake ba”. M Jameel kuwa zama ya gyara tare da fuskantar Innayi da kyau kana cikin wata raunan'niyar Murya ya lumshe idanunsa tare da cewa. “Tunda muke tare daku tsawon shekaru Innayi daga ke har Moddibo ban taɓa ɗaukar abu in baku ku karɓa ba, duk abinda na baku sai kun mayar min dashi baya, ban sani ba wataƙil shi Moddibo yana ɗaukar Maganar Aunty Karima keyi amatsayin matakin ƙin karɓan abu awajena”. Lumshe idanu Moddibo yayi tare da jingina kansa da Murfin motar yana sauraron abinda aminsa ke faɗa. Ita kuwa Innayi idanu ta zuba masa tana nazarin kalamansa. M Jameel ya cigaba da cewa. “Abinda Moddibo bai saniba koya karɓi abu awajena ko karya karɓa ita gani take komai na rayuwarsa Ni nake masa dan haka gwara ma ya karɓa idan yaso ta tuhumesa da tushe”. Ya furzar da iska mai zafi kana ya cigaba da cewa. “Kema kuma Innayi ina ganin maganar mutane kike ɗauka da suke cewa Babana ke daukar ɗawainiyar ku amma ni nasan ba haka bane. Allah ne kaɗai ya barwa kansa sanin yanda kuke rayuwarku duk da aminantakar dake tsakani na da Moddibo har yau ɗin nan bansan taya kuke mu'amala da rayuwarku ba bansan ta yanda kuke samun abinda kuke biyan buƙatar rayuwarku ba kama daga karatun Moddibo kab babu aƙaramar makaranta zuwa hidimar fitanmu Makarantar waje ina sane ina kuma tunawa Naira biyar kun ƙi karɓan tallafi awajen Babana ku keyin komai abinda yasa mutanen gari suke ɗaukar haka suna lura da Moddibo ba wani sana'a yake ba sannan ana mamakin irin buƙatun da kuke yafi ƙarfin samun ku ko kuma tattalin ku Innayi!”. Dariya mara sauti Innayi tayi tare da jinjina kai kana ta tsaida idanunta akan Moddibo daya dafe kansa sai kuma ta kalli M Jameel daya dafe kansa tayi murmushi tare da cewa. “Abun aduhu ne Jamilu barshi kawai babu ɓuƙatar sai ansani, shi kansa Moddibo bai san komai akan al'amuran rayuwar nan ba bare ya gaya maka”. Moddibo kuwa Sanyayyar Ajiyar zuciya ya sauƙe tare da kallon M Jameel ya buɗe masa hannunsa alamar kaji dai nima bansan komai ba a cikin abubuwan da kake son sani. Sai kuma Moddibo ya numfasa tare da lumshe Idanunsa kana cikin sanyin murya mai cike da rauni ya kalli Innayi tare da cewa. “Kagani ni kaina ban san komai ba kama daga lokacin dana ke karatu. Ni dai nasan tana min komai idan nayi magana sai tace gadon Iyayena da suka bar min ne, bansan inda ta ɓoye kuɗin ba na girma ma yanzu ta bani gadona ahannuna taƙi ko gani take har yanzu ban kai ba oho. Kai kuma kana tuhumata kamar acikin aminantakar mu akwai abinda nake ɓoye maka, bayan kuma J ka sani babu wani shamaƙi tsakaninmu”. Ya ƙarisa mgnar tare da runtse idanunsa a take kuma ya buɗe su akan M Jameel da shima shi yake kallo, a hankali ya furzar da iska mai sanyi tare da cewa. “J ba'ayi wani abu na duniya da ni Aliyu zan iya ɓoye maka ba, aminantakar mu ta wuce babin in ɓoye maka wani abu”. Jinjina kai M Jameel yayi yana kallon amininsa cike da tausayawa. Innayi kuwa murmushi tayi tare da jinjina kai amma ba tace komaiba ba. Moddibo kuwa kallon Innayi yayi kana yace. “Yanzu kuma hidimar da nake kai kan ka kasan inda nake samu tunda muna aiki kuma ana biyan mu sannan kuma. Ni kaina wataran saidai inga tayi min abu misali yanzu mota dai ni bansa araina ba kafin in ankara har ta saya anyi komai kafin ma mu dawo”. Numfashi ya sauke kana ya cigaba da cewa. “Babu yanda banyi da ita ta faɗa min ba idan ma a kuɗin gado nane tunda na girma ta bani abuna zan iya sarrafawa”. Hararansa Innayi tayi kana tace. “Anƙi abaka”. Shiru M Jameel da Moddibo kai ya jinjina ba tare da tace komai ba sai tsirawa Innayi ido da sukayi. Miƙewa M Jameel yayi yace. “Bari mu tafi Innayi”. Kai ta gyaɗa tare da cewa. “Allah ya tsare” Suka amsa da. Amin Shi kuwa Moddibo Kallon Innayi yayi kana yace. “Innayi har yanzu yarinyar nan bata zoba?" Jinjina kai Innayi tayi tare da cewa. “Dama wannan shekarar Ummin Asma'u tace in bari zata turo min Asma'u dan ƴaƴan ƙabilun in sun zo gaba ɗaya lalata sukeyi sannan basajin magana to Asma'u zata zo ta tayani”. Cikin kula ya kalli Innayi kana yace. “Innayi anya Asma'u zata iya ayyukan da suna da yawa fa kinga akwai abincin da za'a dinga fitarwa na masallaci”. Jinjina kai Innayi tayi kana tace. “Zamu iya ai naga Asma'u tana da kuzari kuma nima da kuzarina da kuma lafiyata zan iya”. Kai ya gyaɗa kana yace. “Toh Allah ya temaka”. Ta amsa da. “Ameen”,Kana tace. “Ai girkin ma na iya tsawon kwana goma sha biyar ne zamuyi”. Kai M Jameel ya Jinjina kana yace. ”Eh haka ne Innayi”. Sallama suka mata sannan M Jameel ya Miƙe. Dama already Moddibo na cikin motar yaja suka tafi. Kai tsaye kasuwa Moddibo ya sake nufa Kallonsa M Jameel yayi kana yace. “Mai zamu kuma yi a kasuwa?". Ba tare da Moddibo ya juya ya kallesa ba ya lumshe idanunsa kana yace. “Idan muka je za kaga ni”. Shiru M Jameel yayi har suka isa kasuwar kamar yanda Moddibo yayiwa Innayi siyayya haka ya sake sayan wasu Kallonsa M Jameel yayi tare da cewa. “Wannan kayan na waye haka?”. Anutse Moddibo yace. “Ina ruwanka”. Daga haka yaja motar suka fita kai tsaye hanyar gidan Ummi ya nufa. Da sauri M Jameel ya juya ya kallesa kana yace. “Ai baka isa ba Ummi ba zata karba ba ai kai ma idan zan kaiwa Innayi abu hana wa kakeyi”. Moddibo kuwa baki ya taɓe kana yace. “Ai ba Umminka kai ka ɗai bane harda ni dan haka kabarni in samu lada”. Murmushi M Jameel yayi Amma baice komaiba. Koda suka isa aka shigar da kaya, M Jameel yayi wa Ummu bayanin yadda sukayi. Ita kam Ummi sai ta riƙa sakin murmushi bayan ta gama jin jawabin M Jameel sai kuma ta kalli uban kayan da aka shigo dasu ta juya ta kalli Moddibo daya tanƙwashe ƙafafunsa tare da sunkuyar da kansa ƙasa tayi murmushi fuskarta ɗauke da murmushi cike da ƙaunarsu ta saki ajiyar zuciya kana tace. “Ubangiji Allah ya Albarkanci rayuwar ku Ubangiji Allah ya baku ƴaƴan da zasuyi muku biyayya fiye da yanda kuke mana”. Atare suka amsa da. “Ameen”, Bayan sun sake taɓa hira suka miƙe tare da yimata sallama suka tafi...! By *GARKUWAR MARUBUTA* [19/07, 7:44 PM] Halimatu A/rahman Sadeeya: 📝✨💫⏰🤴🏻👹❤️❤️❤️🍇 *SAKAYYAH* _Pape 14_ NA *AYSHA ALIYU GARKUWA* 🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 *Free page ne ƴar uwa saura uku kacal mu gama free page, har yanzu baki makaraba ki biya* *Littafin SAKAYYAH na kuɗine ƴar uwa ki biya ki karanta cikin Aminci da salama babu haƙƙin wani kanki. SAKAYYAH 1k ne kacal 0661110170 GTBank AISHA ALIYU GARKUWA, sai ki turo min shaidar biyanki ta WHATSAPP 09097853276. Kana sai in saki a Group, ɗin da zan rinƙa posting.* *WOHOHO IN KAJI ANA ƘI GUDU TABBAS SA GUDU NE BEZO BA* _Ina kuke Ma'aurata masu sha'awar ganin sun zama taurari kuma fitilu a idanun mazajensu Uwar gida,Amarya,Tsakar gida,hadda tan kaɗen gida Shararriya kuma ƙasaitacciya data saba kawo muku nau'ikan sirrin sahihan magungunan ma'aurata wato *AYSHA ALIYU GARKUWA* Garkuwar Marubuta ayau ma ta dawo muku da Ingantattun magungunan mata masu kyau da inganci domin gyara kanki ki zamto tauraruwa a idanun mijinki...Muna da Ingantattun Abubuwa kamar haka_ :_Munada Garin mallaka, garin maɗi, garin Hakkin mayi, garin ɓelɗamhi Garin ilanwaddihi, Gumbar da ba'a baiwa mai kishiya, Gumbar kolli mai kellin al'khairi, Gumbar Riɗi wato 3 in 1, Gumbar makwaranyi, Masin Maliƙi mai masifar ƙarfi da matse mace, ka masin Daɗi har Maɗigan Akwai, kwanon ƙasaitacciyar mace mai masifar kyau da ratsa jiki da samar da inƙantacciyar ni'ima yanada abubuwa masu kyau haɗinsa, Zumar goron tula mai masifar kyau, tsumin dabino, mai ratsa jiki, tsumin Riɗi mai ƙarfi, Furar Mata mai tsastsafo da ni'imantaccen damshi, Cida kaza, Ciccibi Abodi, Tsumin Ɓaure, tuwon ɓauren, kana akwai maganin sanyi sadidan, da dai sauransu...Se kuma fannin ƙamshi kasance da Shu'umin ƙamshi wanda ze gigita ƙwaƙwalwar Oga tare da jin ko wacce mace bata kaiba...._ _Shin ko kina da labarin Miskilinci da ƙasaitar Rayyan Naaan amma lokaci ɗaya ya zamto zautacce sakali akan soyayyar Jannart bakomai Jannart ta riƙe ba face sirrinkan gyara da kuma shu'uman humran da kulaccar sirri na Aysha Aliyu Garkuwa(Tubali) tabbas taga tasirin haka domin Naanunta ya zame mata tamkar bawa_ _Shin ko kinsan sihirtaccen haɗin da Aysha ke sha kenan ta zamto tauraruwa a idanun Hamma Yusuf(Miwasmiti)...Tabbas Mahmud ya zamto zautacce kuma makaho akan sauyayyar Bazawara wato khadijarsa duk da kuwa gashi da budurwa(Namiji Baya Kaɗan) ko kinsan hakan nada alaƙa da amfani da sahihan maganin da kuma shu'uman humran Aysha Aliyu Garkuwa??.Nasan ba zaka ku manta da irin kima da kuma darajar da Aysha ke dashi acikin Idanun Sheik Jabeer ɗin ta duk da kuwa shekaru sunja anma jinta yake tamkar budurwa 'yar sha bakwai(Garkuwa) sirrin hakan na tare da Ingantattun kuma sahihan magungunan Aysha Aliyu Garkuwa Wato Garkuwar Marubuta da kuma Ma'aurata na tabbata kunsan da cewa basirarta ba'a iya rubutun littafi ya tsaya ba hadda inganta rayuwar ma'aurata ta hanyar kawo musu Nagartattun abubuwa Ga duk wacce ta shirya saya seta tuntuɓi number ta 09097853276 muna iya tura kayan mu aduk inda kuke afaɗin Nigeria harma da ƙetare Dan Allah 'yar uwa idan baki shirya siyaba kada kiyi min magana muɓatawa kanmu lokaci...._ 🤝🏻🤝🏻🤝🏻🤝🏻🥰😘sai.kunzo. sayan na gari maida kuɗi gida, Washe garin washe gari. Da daddare watan Ramadan ya bayyana. Haka yasa dukkan ɗauka cin Musliman duniya suka cika da farin ciki tare da yin niyan ɗaukar azumin watan Ramadan ɗin, kana kowa yana shirya bukatunsa dan miƙa su ga Ubangiji Mabuwayi gagara Misali. Washe gari Ranar Litinin gaba ɗaya al'ummar Musulman duniya sun tashi da azumin watan Ramadan abakinsu gaba ɗaya ɗaukan farko ɗauka ɗaya akayi duk duniya abinda aka daɗe ba'a yiba tsawon lokaci mai yawa wannan shekarar ansamu kowa na cike da farin cikin wannan al'amari azuciyar musulmai. Da daddare Misalin ƙarfe 9:00 pm Babban masallacin juma'a dake ƙofar gidan Sarki cike yake da. Al'ummar Musulmi maza da mata wanda duk shekara idan aka shigo Ramadan bayan an idar da sallar isha'i M Jameel da Moddibo ke gabatar da Tafseer Alkur'ani mai girma duk shekara Moddibo ke jan baƙi yayin da M Jameel keyin Tafseer yana fassarawa. Masha Allah kamar yanda suka gabatar ashekarar Bara ayau ma hakane Cikin Masallacin Maƙil yake da dubban jama'a yayin da Moddibo ke zaune akan wani ƙayatenccen kujera gabansu babban table ne dake ɗauke da system jikinsa sanye da Jallabiya Armygreen mai yauƙi da sansti kana gaba ɗaya ilahirin jikinsa na fitar da sanyayyan ƙamshi tularensa, idanunsa alumshe yana motsa laɓɓansa alamar tasbihi yake. Yayin da M Jameel ke zaune gefensa cikin shiga na alfarma Bugaggiyar shadda ce fara sol anyi masa ɗin kin ƴar ciki da gariya sai hula baƙa sosai yayi kyau gaban jikin rigarsa maƙale da microphone. Cikin tsantsar nutsuwa da kamala M Jameel ya hura microphone ɗin tare da gyara zamansa kana yace. _“A'uzubillahi Minal Shaiɗanir rajeem Bismillahir Rahmanir Rahim. Innal hamdillah Nahmud wanastainuhu wanastaghfiru, wa'nazubillahi min shuriri anfusna, wamin sayyi ati a'amalina, manyah dillahu fala mudillah waman yudil fala hadiyala, Wa'ash hadu Allah ilahalillahu wahdahu lasharika lahu Wa'ash hadu Anna Muhammad Abduhu warasuluhu._ Ya ɗan sauƙe numfashi tare da sauƙe numfashi kana ya sakin ajiyar zuciya sannan ya cigaba da cewa. _“Ya ayyuhallazina amanut taƙullaha haƙƙu tuƙatihi wala ta mutunna illah wa'antum Muslimun ya ayyuhan nabiyu taƙu rabbakummalazi wahida wakalaƙa minha zaujuha wabassa min huma rijalan kasiran wani sa'a wattaƙullahal lazi tasa aluna bihi wal arhama innalaha bikum kana alaikum raƙibaaa_ Baki ɗaya ciki da wajen masallacin ya kacame da sowa da sassarfan waɗanda ke harabar masallacin da suke shigowa da sassarfa. M Jameel kuwa idanu ya lumshe tare da buɗesu kana yace. “Amma ba'ad faya Ikhwatul musulmi Assalamu alaikum Warahmatullah Wabarkatuhu”. Gaba ɗaya cikin masallacin da harabarsa suka amsa da faɗin. “Wa'alaikum Salam Warahmatullah wabarkatuhu”. Gyara zama M Jameel ya yi tare da kallon ɗumbin jama'ar dake masallacin kana a hankali ya numfasa sannan yace. “Insha Allahu zamu cigaba da Tafsirin Alkur'ani mai girma kamar yadda muka saba, zamu kuma ɗaura daga inda muka tsaya bara. A cikin suratul Nisi'i awancan shekarar mun tsaya akan aya na ɗaya wanda ya zamana shi muka karanta Ramadan ya ƙare cikin ikon Allah gashi ya sake sada mu acikin watan wanda da yawa wasu daga cikin wanda mukayi tafsiri dasu wancan shekarar yanzu basa nan kana da yawa wanda muka fara ayau da ƙyar zamu ga ƙarshen amma muna roƙon Allah daya nuna mana ƙarshen wannan wata mai falala da kuma al'barka lfy”. Baki ɗaya wajen suka amsa da faɗin. “Ameen”. Domin wasu daga cikin masu sauraron karatun suna zuwa ne saboda yanda M Jameel ya ƙware awajen Tafseer gashi kuma yana da zafi nama da kwarjinin tafsir. Juyawa M Jameel yayi tare da kallon Moddibo da kansa ke ƙasa ya tsirawa System ɗin sa idanu ya gyara zamansa tare da cewa. “Bismillaha Alaramma jeka cikin Suratul Nisa'i ka karanto mana muji abinda Allah ma ɗauka kin sarki yake faɗa”. Jinjina kai Moddibo yayi tare da gyara zamansa kana ya jingina bayansa da jikin kujera sannan ya lumshe idanunsa cike da nutsuwa ya motsa laɓɓansa kana yayi gyaran Murya cikin Sanyayyar muryarsa mai daɗin saura da sanya nutsuwa da ratsa zuciyar bani adam ya fara kamar haka; “Bismillahir Rahmanir. Gaba ɗaya illahirin yaƙin da sautin muryarsa ya ratsa kunnuwansa, sit sukayi babu abinda wani sauti ko hayaniya, wurin yayi sit kai kace babu mai rai a wurin bare numfashi, gaba ɗaya an nitsu, wanda hakan kuma a jinin Modibbo yake, duk hayaniyar wuri muddin yayi basmalla a take kab za'a nutsu. Idanunsa ya ɗan lumshe kana ya buɗe su a hankali yana kallon taron al'ummar Annabi dake tare maƙil, cike da nitsuwa ya fara karatu cikin zaƙin murya ya kawo aya ta biyu cikin suratul Nisa. .2-Wa'atul ystamaa amwalahum,Wala tatabaddalul khabisa biɗɗayyir,Wala ta'akuluu Amwalahum Ila amwalikum,Innahu kana huban kabira”._ Atake mutanen da masallacin suka shiga lumshe idanunsa yayin da wasu suka shiga sakin ajiyar zuciya Moddibo mutum ne mai ƙwarjini duk yanda waje keda hayaniya da zaran sautin muryarsa ya fita zakaji wajen yayi stit. M Jameel kuwa ya Jinjina kai yayi yana mai jin ayan na ratsa sa cikin yanayin faram-faram ɗinsa yace. “Gabaaa jeka aya ta gaba Aramma muji mai Allah yace”. Sanyayyar iska mai sanyi Moddibo ya furzar tare da gyara zamansa kana ya cigaba da jan Ayar kamar haka; _3-Wa'in hiftum Allah tuƙsiɗu fil yatama fankihu ma ɗabala lakum Minal Nisa Masna wasulasa waruba ,Fa'in hiftum Allah ta'adilu fawahidatan Auma malakat aymanukum,Zhalika adnaa Allah ta'aluun_. Cikin jin daɗin sauraron muryarsa mafi yawan Ƴan matan dake sauraron karatun suka lumshe idanunsu suna burin Allah ya mallaka musu shi amatsayin mijin Aure.Yayin da magidanta suke burin ƴaƴan su suzama kamar Moddibo. Cikin ɗaga sauti M Jameel ke gyaɗa kansa kana yace. ”Je gaba Aramma muje gaba muji me Ubangiji yace” Ajiyar zuciya Moddibo ya sauƙe tare da jingina bayansa ajikin kujera kana ya lumshe Idanunsa tare da gyara system dake gabansa ya cigaba. _“4-Wa'atunnisa'a saduƙatihinnah Nihylah,Fa'in ɗibna lakum anshay'in minhu nafsa fakuluhu hani'am mariyya.5-Wala tu'utussahafa'u Amwa lakumallati ja'alallahu lakum ƙiyama warzuƙuhum fihaa warkusuhum waƙulu lahum ƙaulan ma'arufah”_. Ya ƙarashe jan ayar cikin zazzaƙar muryarsa. Shiko M Jameel gyara zaman Microphone dake gabansa yayi kana yace. “Masha Allah Aramma”. Atake masallacin ya kaure da kabbara wasu na buri da fatan Allah ya azurtasu da baiwan murya irin na Moddibo da yawa daga masu zuwa Tafseer ɗin suna zuwa ne Saboda zaƙin muryan ƙira'ar Moddibo da kuma nutsuwarsa musamman yanda Laudspeaker ke fitar da zazzaƙan murya Moddibo tare da sanya nutsuwa, M Jameel da Moddibo sun iya Tafseer domin shi M Jameel mutum nai mai zafin jini Moddibo kuma ya kasance mutum mai sanyi komai nasa cikin nutsuwa yake hakan yasa mutane ke matukar ƙaunar Tafseer ɗin su mutane kan tsallake unguwar su suzo su saurari nasu. M Jameel kuwa cike da tsantsar ƙwarewa da kuma sanin abinda yake yi ya fara tafsirin ayoyin bayan yayi muƙaddima ya fara fassarar kamar haka : _”Aya ta(2) Allah madaukakin sarki nacewa (Kuma ku baiwa marayu dukiyoyinsu kuma kada ku musanya mummuna da mai kyau.kuma kada kuci dukiyoyinsu zuwa ga duniyoyin ku, Lalle shiya kasance zunubi ne mai girma”_ Mafiya yawan mutanen dake wajen jikinsu ne yayi sanyi domin ji sukayi Ayar tamkar dasu take magana cike da nutsuwa suke sauraren. M Jameel ya numfasa kana ya cigaba da cewa. _“Aya ta (3) Allah yana cewa. _Kuma idan kunji tsoron ba za kuyi adalci ba acikin marayu to(akwai yadda za'a yi)ku auri abinda yayi muku dai-dai daga mata biyu-biyu,Uku-uku ko huɗu-huɗu sa annan idan kunji tsoron baza kuyi adalci ba to ku auri guda ɗaya ko kuwa abinda hannayenku na dama suka mallaka.wannan shine mafi kusantar zama baku wuce haddi ba”._ Numfashi wasu daga cikin mata masu kishi suka saki jin Allah da kansa ya bawa maza ikon su ƙara aure yi shin to wai menene abin kishin hauka duk da cewa dole ne ayi kishi amma ya kamata su rika sassauta. M Jameel kuwa juyawa yayi tare da kallon Moddibo daya zubawa system ɗin sa idanu numfashi ya sauƙe cikin yanayin zafin jinjinsa ya cigaba da cewa. _“Acikin aya ta (4). Allah Mabuwayi gagara Misali cewa yayi. Kuma ku baiwa mata sadakin su sauƙin bayarwa sannan idan suka yafe muku wani abu daga gareshi a daɗin rai to kuci shi da jin daɗi da saukar da hadiya”._ Ya ɗago kansa tare da kallon jama'ar dake masallacin cikin ɗaga sautin murya ya gyara zaman hular dake kansa kana yace. “Kai Kuce Allahu Akbar”. Atake masallacin ya ɗauki kabbara da faɗin Allahu Akbar Allah ya ƙara maka nisan kwana. Murmushi yayi tare dasa hankie ya goge gaban goshinsa kana ya cigaba da cewa. _“Kada ku baiwa wawaye dukiyar ku Wanda Allah ya sanya ta agareku kuna tsayuwa (ga gyaranta)kuma ku ciyar dasu cikinta,kuma ku tufar dasu kuma ku gaya musu magana sanyayya ta alkhairi”_. Atake masallacin ya jure da kabbara cike da jin daɗin tafsirin. Agefen ɓangaren mata Asma'u ce zauna tare da Innayi sai Khausar dake can gabansu Matsawa Asma'u tayi tare da taɓa bayan Khausar,juyawa Khausar tayi ganin Asma'u yasa tayi murmushi tare da miƙewa daga inda take ta dawo kusa da Asma'u. Tana murmushi ta gyara zamanta tare da cewa. “Asma'u ya Ummi amma ɗazun da mukayi waya baki ce min zaki zo Tafseer ba”. Murmushi Asma'u tayi kana tace. “Ai nadawo gidan Innayi da zama zan riƙa taya ta aiki sai Azumi ya ƙare zan koma gida”. Bata jira jin Abinda Khausar zata ceba ta juya tare da kallon Innayi data tattara nutsuwarta zuwa ga tafsirin da jikokin ta keyi hannunta Asma'u ta riƙe kana tace. “Innayi ga Khausar ƙawata”. Murmushi Innayi tayi tare da kallon Khausar,Ita kuwa khausar ƙasa tayi da kanta cike da nutsuwa ta gyara zaman hijabinta kana tace. “In wuni ya ibada?”. Murmushi Innayi tayi tare da cewa. “Lafiya lau Alhamdulillah". Haka nan Khausar taji tsohuwar ta burgeta Kallon Asma'u tayi cikin ƙasa da murya ta kalli Asma'u tare da cewa. “Wacece?”. Asma'u na murmushi ta juya ta kalli Khausar kana tace. “Kakar Moddibo ce”. Taɓe baki Khausar tayi kana tace. “Itakam tana da kyawawan hali ba iri jikanta ba ko ina ya gado baƙin zuciya ohon mishi mugu”. Dariya Asma'u tayi amma batace Komai ba. Bayan M Jameel yayi tafsirin Ayoyi guda goma,ya duba lokaci ganin ƙarfe goma saura minti takwas ya numfasa tare da faɗin. “Wasubhanakal Lahumma wabi hamdi Nash'hadu Allah'ila ha Illah anta nastagfirka wanstubu Ilaik”. Ya rufe system ɗin sa tare da cewa. “Dan Allah kamar yanda aka saba maza suyi haƙuri mata su fara fita”. Sai da duk matan suka gama fita kafin maza acan mota Innayi da Asma'u suka jira M Jameel da Moddibo har gida aka kaisu bayan sun isa gidansu Moddibo kasancewar duk Ramadan agidansu Moddibo M Jameel keyi saboda yawan hidimarsu. Suna isa kai tsaye sashen Moddibo M Jameel suka nufa Asma'u da Innayi kuwa sashen ta suka nufa suna shiga ciki Innayi ta cire dogon hijabin dake jikinta tare da kallon Asma'u tana ajiye hijabin ta sauƙe ajiyar zuciya da faɗin. “Asma'u ɗauki abinci ki kaiwa Yayunki tun da akayi buɗa baki ƴaƴan itatuwa da kunu kaɗai suka sha basu ci wani abu ba”. Jinjina kai Asma'u tayi kana tace. “Toh”,Sannan ta ɗauki Faranti Perpesoup ɗin kaza,da Couscous da miyan ƙwai sai perper cheking sai juice ɗin Abarba da kwakwa sai kuma fruit salad. Bakinta ɗauke da Sallama tashiga zaune ta same su M Jameel na kan 2sitter yayin da Moddibo ke kan 3sitter Idanunsa alumshe ajiye wa tayi tare da juyawa zata fita. M Jameel ya ɗago kansa tare da kallon Asma'u dake shirin fita yace. “Asma'u zo ki zuba mana yunwa nakeji wallahi kinsan Magana ba wasa ne dashi ba”. Murmushi tayi kana tace. “Hakane”. Kam sannan ta tsugunna ta buɗe Warmers din Atake ƙamshi ya bugi hancinsu da sauri M Jameel ya Kalli Asma'u tare da cewa. “Asmeey wayayi wannan girkin?”. Tana zuba musu miyar ƙwoyin akan Couscous ɗin ta ta ajiye kana tace. “Ya Jameel nice Nayi”. Ware ido M Jameel yayi. “Kai Asmeey ki faɗi gaskiya dai”. Murmushi tayi da faɗin. “Allah da gaske ni nayi yaya Jameel”. Abincin ya ɗiba ya kai bakinsa tare da lumshe idanunsa kana yace. “Waya koya Miki wanna girkin?”. Dariya tayi kana tace. “Khausar ce ta koya min Allah yaya Jameel yawanci idan naje gidan take koya min”. Moddibo dake kwance ya harareta kana yace. “Ke dai Arayuwarki komai baki iya ba sai dai wata ce ta koya miki, ki bari mana akoya mikin kawai akayi ba magana ta ƙare ba ba sai kince ga wacce ta koya miki ba”. Ya ƙare maganar kamar bashi yayi ba. Murmushi Asma'u tayi kana tace. “Allah Yaya Moddibo Khausar ta iya girki sosai saboda kullum tare suke shiga kichen da Mommy ta”. Baki ya taɓe da faɗin. “Naji jeki ki gaida Innayi”. Kai ta gyaɗa tare da yin murmushi har ta kai ƙofa zata fita sai ta kuma ta sake juyawa tare da komawa ciki kana tace. “Yaya Jameel ƙofan Innayi babu wata gashi kuma naga nan akwai wuta”. Moddibo dake kwance ya shafa sajensa kana yace. “Itace tace bata so gashi har cikin kicin ɗinta taƙi a kaishi ɗakinta”. Baki Asma'u ta tura tare da Marerece fuska kana tace. “Nikam gaskiya zama ba wutan nan baimin ba”. M Jameel dake cin Chicken Peper ya kalleta tare da cewa. “Toh kije ki faɗa mata wata ƙil wala Allah idan ke kin faɗa ta yarda asa mata”. Kai Asma'u ta jinjina kana ta miƙe tare da faɗin. “Toh”,Sannan ta fice ta nufi sashen Innayi. Bakinta ɗauke da Sallama tashiga ɗakin Innayi zaune ta samu Innayi da lantarta azaune hannunta riƙe da carbi tana ja. Zama tayi daga gefen Innayi kana tace. “Innayi naga an kawo wuta a sashen su Yaya Moddibo Nan kuma babu wallahi rashin wutar nan beyi ba”. Anutse Innayi ta juya ta kalleta kana tace. “Ayyah Asma'u am ni tsoron wutan nan nake ji bana son irin wannan abubuwan ke kuma kina so ko?”. Jinjina Kai Asma'u tayi tare da faɗin. “Allah Ni dai inaso”. Innayi ta kalleta kana tace. “Zafi kike jine?”. Girgiza kai Asma'u tayi tare da cewa. “Ba zafi ba haske dai Innayi ɗan tv nan dai idan alasa zamu riƙa kallon sunna Tv”. Jinjina kai Innayi tare kana tace. “Shikenan sai asaka tunda haka kike so insha Allah gobe zan faɗa musu asaka mana”. Da sauri Asma'u ta miƙe kana tace. “Bari Inje in faɗa musu yanzu”,Ta ida maganar tare da ficewa. Kai tsaye sashen ta koma bakinta ɗauke da Sallama tashiga Idanunta akan Moddibo dake kurɓan Juice ɗin fuskarta ɗauke da murmushi kana tace. “Yaya Moddibo Wallahi Innayi ta yarda aja mata wuta kuma dan Allah asamar mana Tv zamu riƙa kallon Tafseer kaga ita yanzu sai dai tayi ta rungumar Radio komai sai dai taji ta Radio”. Jinjina kai Moddibo yayi kana yace. “Toh shikenan Allah ya kaimu goben”. M Jameel kuwa kallon Asma'u yayi fuskarsa ɗauke da murmushi ya ajiye Plate ɗin hannunsa kana yace. “Tafff lallai Asma'u ke ta musamman ce kinyi babban sa'a babu yanda ba muyi da ita ba muja mata wuta taƙi”. Murmushi Moddibo yayi kana yace. “Ai Asma'u ta hannun daman Innayi ce”. Murmushi Asma'u tayi tare da ficewa ta koma falon Innayi suka kwana Misalin biyu da rabi Innayi ta farka kana ta tashi Asma'u suka fita alwala sukayi suka gabatar da nafilla tare da adduo'i ƙarfe uku dai-dai Innayi da Asma'u suka shiga kichen Innayi tayi musu ɗumanen tuwan jiya tare da tafasa ruwan shayi daya ji kayan ƙamshi sai kuma ta ɗumama perpesoup ɗin kazan ita kuwa Asma'u attaruhu da albasa ta jajjaga tare da ɗauraye tukunya ta sanya akan gas wanda zuwan Asma'u ne Moddibo suka kawo mai ta zuba kana ta zuba jajjegen tare da zuba spices da Maggi da kuma Curry ta zuba kana ta zuba sanwa Bushesh-shen kifi dake gyare ta zuba sannan ta ɗauƙi carrots,da grean beans,da kuma cabbage ta shiga gyarawa jin ruwan na tafasa ta tsaya ta zuba Spaghetti leda ɗaya sannan ta cigaba da gyarawa sai daya kusa tsotsewa sannan ta zuba cabbage,grean beans,Carrot,aciki Nan da nan gidan ya kaure da ƙamshi Warmers ta ɗauka ta juye sannan ta zuba sauran a plate ta haɗa kayan duka a babban faranti ta ɗauka bakinta ɗauke da Sallama tashiga falon. Moddibo dake zaune riƙe da Alkur'ani ya ɗago kansa tare da amsa Sallamar bayan ya kai ƙarshen ayan Moddibo kuwa idanunsa ya ɗauke daga kan system ɗin tare da kallon Warmers din sai kuma ya Kalli Asma'u dake ajiyewa akan center table ya shafa sajensa tare da cewa. “Asmeey ya naga kuloli da yawa haka?”. Murmushi tayi kana tace. “Wannan ɗumame ne Innayi tayi muku ɗayan kuma ɗumamen perpesoup ɗin jiya ne wannan kuma jollof nayi muku na Spaghetti”. Jinjina kai M Jameel yayi kana yace. “Ni dai kamar nafi son ɗumamen Amma bari naga jollof ɗin naki”. Ya ida maganar tare da buɗe Kulan cikin sauri ya lumshe idanunsa jin ƙamshin daya ratsa hancinsa. Kallonta yayi kana yace. “A'a bazan ci ɗumame ba”. Juyawa Moddibo yayi tare da kallon M Jameel kana yace. “Ai kuwa baka Isa ba ɗumame zaka ci, Asma'u Allah ya miki albarka”. Sai kuma ya sake kallon M Jameel dake murmushi kana yace. “Ai dolenka ɗumame zaka ci dan kaine Innayi ke yin ɗumame ko wani shekara sai ka ishemu da ɗumame saboda kai ake liƙa mana”. Murmushi M Jameel yayi kana yace. “Ai ɗumamenta yana da daɗi kai kan ka in faɗa maka zakayi missing ɗumanenta idan baka kusa yanzu ma dan kana tare dashi ne”. Murmushin gefen baki Moddibo yayi kana yace. “Um naji amma dai yau shi zaka ci”. Dariya M Jameel yayi tare da cewa. “Ba matsala ai ɗumamen Innayi nace”. Miƙewa Asma'u tayi tare da ficewa Moddibo da M Jameel kuwa Matsawa sukayi tare da fara cin ɗumamen kaɗan suka ci sannan suka ci jollof ɗin taliya suka sha tea perpesoup din kazar kuwa ko buɗewa basuyi ba bayan sun gama suka miƙe suka tafi masallaci tare da idar da sallah saida sukayi Azkhar kafin suka dawo gida suka kwanta bacci kafin wani lokaci su tashi su tafi Tafseer acikin makarantar su. Ƙarfe Goma da rabi dai-dai suka farka atare Moddibo ya miƙe bakinsa ɗauke da addu'a kana yashiga toilet yayi wanka tare da daura al'wala zama yayi tare da shafa lotion mai ƙamshi sannan ya sanya Jallabiya Marron colour tare da ɗaura baƙin Alkyabba akai kana ya naɗa hirami akansa sosai yayi kyau tamkar balarabe kana ya feshe jikinsa da turarukansa masu daɗin ƙamshi sallah walha ya gabatar tare da zama ya fara ƙira'a cikin Suratul Maryam. Sha daya da rabi dai-dai M Jameel ya fito daga ɗaya Bedroom din cikin shiri da alama ya gabatar da sallar walhar shima kallon hadaɗɗen agogon dake ɗaure atsintsiyar hannunsa yayi kana ya maida kallonsa kan Moddibo tare da cewa. “A.J sha biyu ta kusa fa mutafi kasan ana jiranmu”. Dai-dai lokacin da wayar Moddibo yayi ruri kallon screen ɗin yayi tare da kallon M Jameel kana yace. “Gashi ma malam Arɗo ke kirana da alama zai ce mu ake jira masallaci ya cika”. Jinjina kai M Jameel yayi kana yace. “Mu tafi”. Kai Moddibo ya gyaɗa tare da ɗaukar mukullin motar suka fice. Kai tsaye masallacin dake cikin makarantarsu suka nufa wanda yake cike da maza da mata ko wanne na ɓangaren su sai dai mata sunfi yawa ƙarfe 12:00 ya musu acikin masallacin. Gyaran Murya M Jameel yayi cikin nutsuwa da kuma yanayin zafin jinjinsa ya gyara zamansa tare da cewa. _“Innalhamdulillah Nahmaduhu Wanastainuhu wanastaghfiru wa'nazubillahi billahi min shuriri anfusna wamin sayyi ati a'amalina manyah dillahu fala hadiyala waman mudillah fala hadiyala Wa'ash hadu Allah ilahalillahu Wa'ash hadu anna Muhammadu Abduhu warasulu amma ba'ad faya Ikhwatul musulmi Assalamu alaikum warahmatullah wabarkatuhu”_. Suka amsa da. “Wa'alaikum Salam warahmatullah wabarkatuhu”. Ya numfasa tare da kallon Moddibo da idanunsa ke lumshe sai kuma ya gyara zamansa kana yace. “Duk kan yabo da godiya su tabbata ga Allah subhanahu wata'ala mai kowa mai komai daya sake nuna mana wannan wata mai cike da falala da kuma rahma Allah ya nuna mana ƙarshen sa lafiya kamar yanda ya nuna mana farkon sa Awancan shekarar mun tsaya aƙarshen Suratul Jinni insha Allah yau zamu ɗaura acikin Suratul Muzammil Aramma jeka cikin suran muji mai Allah yace”. Gyaɗa kai Moddibo yayi tare da gyara zamansa cikin nutsuwa da sanyin Muryansa tare da kamala kana yayi A'uziyya tare da basmala ya fara kamar haka;. _“1-Ya Ayyuhal Muzammil,2-Ƙumullaila illa ƙaliliah 3-Nisfshu awinƙus minhu ƙalila”_ Atake masallacin yayi tsit tamkar babu mahalukin dake numfashi yayin da karatun ke ratsasu. Shikuwa M Jameel Kai ya gyaɗa da faɗin. “Yawwa Aramma ci gaba mai Allah yake cewa acikin aya ta gaba”. Jinjina kai Moddibo yayi tare da manna bayansa da jikin kujera ya cigaba da cewa. _“4-Auzidhu alaihi warartilill ƙur'ana tartila5-Inna sanulƙi alaika ƙaulan sakila”_. Numfashi M Jameel yayi kana yace. “Suratul Muzammil Makiyya ce tana da ayoyi guda ashirin. Ya numfasa tare da lumshe idanunsa kana ya cigaba da cewa. “Suratul Muzammil tana karantar da tarbiya da juriya ga Muslimi,domin susami damar tsayuwar da umarnin Allah”. Still wajen yayi tamkar babu mahalukin dake numfashi jama'ar dake wajen su tattara duk kan nutsuwarsu suna sauraron abinda Allah yace Moddibo kuwa System ɗin gabansa ya zubawa Idanu tare da lumshe idanunsa. M Jameel ya numfasa tare da cewa. _“Ya Ayyuhal Muzammil,Ma'ana ya kai wanda ka lulluɓa da mayafi”_ Atake masallacin ya kaure da kabbara suna faɗin. “Allahu akbar, Allahu akbar Allah yakareka Malam”. Zama M Jameel ya gyara tare da kallon jama'ar bayan sunyi shiru ya ɗaura da cewa. _“ƙumillayla illa ƙalila,katsaya domin yin Sallah acikin dare(suka) face kaɗan”._ Nanma kabbara suka sake kaurewa dashi. Shi kuwa M Jameel numfashi ya sauƙe kana ya cigaba da fadin. _“Nisfshu awin minƙushu ƙalila,Rabinsa ,ko ka rage Abu kaɗan daga gareshi._ Haka suka cigaba da tafsirin ayoyin. Ƙarfe ɗaya dai-dai suka tashi ɗaya da kwata sukayi Sallar azahar zama sukayi acikin masallacin suka fara Muraja'a tun daga suratul tauba zuwa Nahal jin kiran la'asar yasa suka dakata kana suka tashi Moddibo ne yaja Sallar M Jameel kuwa shi yayi ladanci bayan sun idar ne suka fita kai tsaye masallacin dake Unguwar su Moddibo suka nufa ƙarfe biyar suka fara gabatar da tafsirin acikin suratul hujurat wannan kuma na maza ne zalla ƙarfe shida dai-dai suka tashi. Bayan sun tashi M Jameel yashiga mazaunin Driver Moddibo kuwa gefen mai zaman banza ya zauna tare da lumshe idanunsa yana sakin numfashi Kallonsa M Jameel yayi tare da murmushi kana yayiwa motar key. Wayar Moddibo ne ya hau ruri Anutse ya sanya hannu ya ɗauka ganin sunan Ummi yasa ya gyara zamansa cike da nutsuwa yayi Picking tare da Sallama kana yace. “Ummi ina yini”. Daga ɗaya ɓangare cike da so da kulawa Ummi tayi murmushi kana tace. “Babana". Moddibo ya amsa da. “Na'am Ummina”. Murmushi Ummi tayi tare da cewa. “Babana sannuku da ƙoƙari nasan yanzu baki da hutu Ramadan ya shigo”. Jinjina kai Moddibo yayi kana yace. “Ga munan dai kam Ummi muna fama”. Cike da kulawa da kuma ƙaunar su tace. “Allah sarki Allah ya biya ku Allah yaƙara rufa asiri”. Ya amsa da. “Ameen”. Ummi ta gyara wayar akunnenta kana tace. “Babana nashirya muku abin buɗa baki kuzo kusha ruwa”. Kai Moddibo ya gyaɗa kana yace. “Toh Ummi mun gode muna nan tafe yanzu ma Insha Allah zamu zo”. Kasancewar M Jameel na Jin Komai saboda wayar a handsfree yake yasa ya juya akalar motar zuwa hanyar gidan Ummi adai-dai ƙofar gidan Ummi M Jameel yayi hong mai gadi ya buɗe musu suka shiga...! Yau dai ba editing. Dan muna cikin hidiman bikine By *GARKUWAN MARUBUTA* [19/07, 7:44 PM] Halimatu A/rahman Sadeeya: 📝✨💫⏰🤴🏻👹❤️❤️❤️🍇 *SAKAYYAH* _Page 15_ _NA_ *AYSHA ALIYU GARKUWA* 🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 *Saura ƙiris FREE PAGE dai yazo ƙarshe in sha Allah mun kusa gamawa. Yar uwa ki biya ki karanta cikin Aminci domin littafin SAKAYYAH na kuɗine 1k ne kacal 0661110170 GTBank AISHA ALIYU GARKUWA. Sai ki turo min shaidar biyanki ta WHATSAPP. 09097853276. Kana in saki a Groups ɗin da zamuci gaba da posting.* *GARKUWAR* taku ce dai MA'AURATA, da masu shirin aure, da masu jego, da yan gayu masu son k’amshi kece raini, da gyaran da zaike maimaita muku dararen forkon kuruciya* Ko kunsan Jikinmu na da sinadaran hormones da suke taimakawa dan’adam akan komai musamman lokacin da mace take mu’amalar aure da mijinta. Mafi akasari wannan hormones din ne ke samun matsala ko su yi sanyi koma su daina aiki kwata-kwata shi ne dalilin da zai sa mace tace bata jin sha’awa ko bata san dadin aure ba. Albishirinku ina da kayan da ke taimakawa wannan sinadaran du dawo aiki tukuru don karkato miki da kimarki wajan mai gida sannan su taimakawa wannan sinadaran hormones dinki su dinka secreting din ni’ima wadatacciya da zata taimaka miki ki gamsu mijinki ya gamsu fiye da tunaninki. Note: Kayana ba sa tsinka ruwan ni’ima suna dai taimakawa hormones dinki ne su tsattsafo da ni’imar musamman wacca cutar sanyi ko dattin mahaifa ya dankarar da su ya hana su yin aikinsu yanda ya kamata. Haka zalika idan kina da kyau ki kara da wanka. Zaki iya amfani da magani na na gargajiya wanda zai gyara miki sex hormones din kullum ki kasance cikin humidify wato cikin damshi mai albarka kamar yanda ake son mace. Yana gyara miki mara. Sai kamshi. Hajiyata daure ki fara amfani da turarena ki ji irin salon kamshin sa salo ne da zai daidaita ki da mijinki ya kankaro miki da kimarki a wajansa. Siyan na gari mayar da kudi gida. Ga masu buƙata ga number' wayata wanda nake whatsApp dashi 09097853276 kimin mgn ta whatsApp in har kin tabbatar kin shirya saya mu dai-dai ta, kayana ba ƙanana bane, shiyasa bana harkan karanta, muddin kinsan baki shirya sayaba Please kada kiyi min mgn ki bari sai kin shirya kuɗinki a hannu, ba ina nufin kayana bana talaka bane, no akwai ƙananan set na masu karamin karfi, banson aimin mgn a ɓatamin lokacin aiyukana a shirme baki shiryaba. Shine karantan da bana so. 0005388578 Jaiz bank AISHA GARKUWA ALIYU. In kin shirya ga number ta ga kuma account number ta wanda in mun gama mgn zaki turo kudin ki, kana insa miki kaya a mota, duk ƙasar da kike kayana zaije gareki, amman fa in kinada dalilin zuwan nasune🤝🏻sayan na gari meda kudi gida. GARKUWAR MA'AURATA Anutse Moddibo da M Jameel suka fito daga motar dai-dai lokacin da Malam Ahmad ya fito daga harabar gidan ganinsu yasa ya faɗaɗa fara'ar fuskarsa tare da faɗin. “A'a Masha Allah tagwayen Ummi kunzo?”. Murmushi sukayi Atare kana suka ƙara sa kusa dashi. Kallonsu Malam Ahmad yayi fuskarsa ɗauke da murmushi kana yace. “Sannunku da zuwa ku isa daga ciki zan dawo mu gaisa”. Kai suka gyaɗa masa atare kana suka nufi haraban cikin gidan shi kuma ya fice. Bakin su ɗauke da Sallama suka shiga farfajiyar gidan, Kusan a tare suka juyo suka kalli juna lokacin da idanunsu, ya sauƙa akan shimfiɗar ƙaton taburma da Ummi ta shimfiɗe asaman baranda kana ga wani lallausan Chanis capet dake fitar da ƙamshi da wasu manyan tuntuna guda uku ɗaya na tsakiya biyu na gefe da gefe sai manyan tire guda huɗu akai tiren farko na kayan fruit ne kama daga,Tuffa, Inabi, Gwanda, Dabino, Abarba, Ayaba, Kankana, Lemo duk anyi slinzing ɗinsu. Ɗaya tiren kuma Flaks ɗin tea ne da ma dai-dai-tan kofina masu kyau sai gongomin madara da Bounvita. Sai kuma ɗayan dake ɗauke da Flaks din kunu agefe, sai kuma na ƙarshe wanda yafi su girma manyan kulo-line masu kyau kula na farko Perpesoup ɗin jan naman rago ne daya dahu ligif yana fitar da ƙamshi sai ɗaya kulan kuma soyeyyen dan kalin ne da ƙwai gwanin ban sha'awa. Jin Sallamar sune yasa Ummi saurin fitowa daga falo tare da faɗaɗa fara'ar dake Samar fuskarta kana tace. “Lale marhaba sannunku da zuwa Babana”. Murmushin gefen baki Moddibo yayi wanda ke ƙara masa kyawun fuskarsa kana ya lumshe idanunsa tare da faɗin. “Barka dai Ummina”. M Jameel kuwa baki ya tura cike da Shagwaɓa kana ya langwaɓar da kai Idanunsa akan Umminsa sai kuma ya kalli Moddibo dake ƙoƙarin zama akan shimfiɗar da Ummi tayi kana yace. “Ni dai gaskiya na fara kishi Ummi mai yasa tun da har haka kike son Aliyun nan bakisa min sunan Babban naki ba nima ki riƙa cemin Babana?”. Murmushi Ummi tayi Idanunta akansa ta zauna kana tace. “To ai kaima Babana ne ko ka manta Kai takwaran kakan kane Baban-Babanka. Dariya mai sauti yayi kana ya shafa sajensa tare da cewa. “Ƙwarai kuwa haka Abbana ke kirana da Babana munyi raba dai-dai Ummi ta kiraka da Babanta Ni kuma Abba na ya kira ni da Babana”. Gyaɗa kai Moddibo yayi cikin yanayin sanyin Muryansa ya Kalli M Jameel kana yace. “Oho dai amma nine na hannun daman Ummi”. Murmushi Ummi tayi cike da ƙaunarsu kana ta zauna daga gefensu Idanunta akan Moddibo dake motsa bakinsa idanunsa alumshe alamar tasbihi yake. Ganin haka sai ta miƙe dan kar ta takura masa ta ɗan ɗaga sautin Muryanta tare da cewa. “Bashir ga Yayanka sun zo baka zo kun gaisa ba”. Cike da ladabi Bashir ya fito kana yace. “Ummi kaya na nake gyarawa yanzu nake so in fito”. Ya Ida maganar tare da zama agefen Moddibo kana yace. “Yaya Moddibo ina wuni ya Ibada?”. Moddibo kuwa buɗe idanunsa dake lumshe ya buɗe tare da ɗaura hannunsa akan Bashir yana shafawa kana yace. “Lafiya lau Alhamdulillah ya karatu?”. Bashir ya amsa da. “Alhamdulillah”,Kana ya maida kallon sa kam M Jameel dake motsa baki da alama shima tasbihi yake ya kallesa tare da cewa. “Yaya Jameel Ina wuni ya ibada?”. M Jameel ya Amsa da. “Alhamdulillah”. Miƙewa Bashir yayi ya koma ya cigaba da aikin da yake. Moddibo kuwa bayan yayi tasbihi sai ya koma Azkharul masa ƙarfe shida da minti Ashirin da biyu aka kira Sallar maghariba Plate din Dabino da Ummi ta ajiye musu agabansu Anutse Moddibo ya miƙe tare da ɗaukan ruwa ya kuskure bakinsa kana ya dawo ya zauna. Shima M Jameel miƙewa yayi ya wanke bakinsa dabino Moddibo ya ɗauka ya buɗe sanan ya sanya abakinsa bayan ya furta. “Zahabazzaba'u Wabitallatil,Uruƙu wasu batul Ajri Insha Allah”. Anutse ya ke cin dabinon inda yaci sai ya sanya ƙwallon atafin hannunsa na hagu. Guda bakwai yaci kana ya dakata. M Jameel kuwa dabino Uku yaci kana ya janyo faranti kayan friut ɗin ya fara da Abarba. Lumshe idanu Moddibo yayi tare da ɗaukar Inabi ya kai bakinsa sai kuma ya buɗe Idanunsa akan Ummin data ƙara so wajen zama tayi tare da tsirawa M Jameel idanu baki ɗaya hankalinta da nutsuwar ta yana kansa. Iska Moddibo ya furzar daga bakinsa tare da jingina bayansa da jikin bangon ya lura da tun zuwansu wani irin kallon da Ummi ke bin M Jameel dashi kallone mai nuni da tsantsar so, da kuma ƙauna da shaƙuwa irin wanda uwa ke nunawa ƴaƴan ta. Ƙasa da kansa yayi yayin da yaji ruwan hawaye masu ɗumi na tsata-tsafo masa saboda ganin shi ya rasa wannan damar bazai samu irin wannan ba arayuwarsa ba still Kansa na ƙasa ba tare daya ɗago ba ya dai-dai-ta muryarsa tare da faɗin. “Ummi kiyi buɗa baki mana”. Sai asannan Ummi ta lura da kallon da take bin M Jameel dashi, Malam Ahmad ma murmushi yayi domin ya lura da kallon da Ummi kebin M Jameel dashi Shikuwa M Jameel sai alokacin ya ɗago kansa ya lura da irin kallon da Umminsa ke binsa dashi. Murmushi yayi mai cike da so da ƙauna. Kana yace. “Ya dai Ummina nayi kyaune ko muni kike ta kallona?”. Ajiyar zuciya ta sauƙe kana ta ɗan lumshe Idanunta tare da girgiza kai kana tace. “A'a kawai dai naga azumi ɗaya akayi ana biyu har ka rame”. Murmushi yayi tare da gyara zamansa kana yace. “Hmmm Ummi kenan ai kinga mu ba azumin ne kaɗai ba. akwai yawon zirga-zirga sannan abincinma bama nutsuwa mu cisa yanda ya kamata musamman ma idan na biyewa Babanki”. Jinjina kai Ummi tayi kana tace. “To yau kam anan sai kunci kuncika cikin ku sannan in dafa muku na Sahur ma ku tafi dashi”. Girgiza kai Moddibo yayi kana cikin sauri yace. “A'a Ummi ki zauna Innayi na mana sannan ga can Asma'u na taya ta yanzu idan mun koma sai mun rasa inda zamu sanya abincin a cikinmu”. Jinjina kai tayi kana tace. “Toh shikenan Babana”. Murmushi Moddibo yayi kana yace. “Ummi kici abinci mana”. Kai ta gyaɗa sannan ta janyo Plate ɗin dabinon ta ci guda uku Bayan tayi addu'ar buɗa baki. Malam Ahmad ma danino uku yaci sannan Ummi ta ɗauki Flaks da niyyar haɗa musu tea Moddibo dake cin friut yayi saurin cewa. “A'a Ummi bari sai munyi Sallah”. Kai ta gyaɗa kana tace. “Toh shikenan sai kun dawo”. Miƙewa sukayi M Jameel da Moddibo suka ɗauki buta kana suka ɗaura alwala suka fice Malam Ahmad kuwa ya riga su fita. Kai tsaye masallacin ƙofar gidan su Ummi da Baban Asma'u ke limancin suka shiga. Suna idar da Sallar Maghariba bayan sun idar suka dawo cikin gida shigowarsu yayi dai-dai da rurin da wayar M Jameel keyi. Kallon Moddibo M Jameel yayi kana yace. “Innayi ce ke kira”. Jinjina kai Moddibo yayi tare da cewa. “Uhm”. picking call din yayi ya kai kunnensa. Daga ɗaya ɓangaren Innayi tayi gyaran murya kana tace. “Jamilu lafiya baku dawo kunyi buɗa baki ba mai kuke yi har yanzu awaje?”. Sajensa ya shafa kana yace. “Innayi wallahi Ummi ce ta riƙe mu wai saidai muyi buɗa baki agidan ta”. Murmushi Innayi tayi kana tace. “Toh mu kuma na gidan mu ya zamu yi dashi”. Kallon Moddibo yayi sai kuma yayi Murmushi kana yace. “Innayi abawa Almajirai dai sai kibar mana na Sahur dan nasan kinyi miyarki mai daɗin nan miyar me kika mana ma tukunna?”. Dariya Innayi tayi kana tace. “Miyar roman da kake so na daddawa da ƙarago shi zanyi muku na Sahur”. murmushi ya saki tare da faɗin. “Yauwa ina son wannan miyar”. Kai ta gyaɗa kana tace. “Toh shikenan sai kun dawo ka gaishe da Ummin”. Ta faɗa tare da katse kiran. Suna ida shiga gidan suka samu wajen suka zauna Ummi ta miƙe tare da ɗaukar Flaks da kofina ta haɗa musu tea mai kauri yana tururi kana ta zuba musu soyeyyen dankali da ƙwai. Anutse suka fara ci kaɗan Moddibo yaci ya janye hannunsa daga ciki. Kallonsa Ummi tayi kana tace. “Ya dai Babana kaci mana”. Murmushi Moddibo yayi tare da ɗaura hannunsa na dama akan shafefen cikinsa ya shafa kana yace. “Ummi na ƙoshi”. Girgiza kai Ummi tayi tare da cewa. “Kai Babana me ma kuka ci?”. Ɗan kwaɓe fuska yayi kana cikin sanyin murya mai kama da shagwaɓa ya lumshe idanunsa tare da cewa. “Ummi kar muje muna sallah abinci yan fitowa ta hancin mu”. Kallonsa Ummi tayi tare da murmushi kana tace. “A'a Babana me ma kuka ci da zai zazzago ta hancinku?”. Murmushi yayi tare da shafa sajensa zuwa gemunsa kana yace. “Allah Ummi mun ƙoshi ko ba haka ba J?”. Kai M Jameel ya gyaɗa tare da Hararan Moddibo ya cire hannunsa a Plate din dan kalin. Hira suka sake taɓawa kana Moddibo ya miƙe tare da kallon Ummi kana yace. “Ummi zamu tafi”. Jinjina kai Ummi tayi tare da cewa. “Idan kunyi sallah Isha'i zaku dawo ta nan?”. Girgiza kai Moddibo yayi kana yace. “A'a Ummi sai wani lokaci”. Gyaɗa kai tayi tare da cewa. “Toh ku tafi da kunun nan”. Ajiyar zuciya Moddibo ya sauƙe tare da gyara tsayuwar sa kana yace. “Toh Ummi ina son kunun abamu zan tafi dashi”. M Jameel ya juya ya kalli Ummi tare da langwaɓar da kai kana yace. “Ummi Ni dai ba abani abinda nake so ba”. Cike da kulawa da kuma so ta juya ta kallesa kana tace. “Me kake so?”. Murmushi yayi kana yace. “Inabin za'a bani in tafi dashi”. Saurin Kallonsa Moddibo yayi sai kuma ya juya ya kalli Ummi tare da cewa. “Ummi kar ki basa yasha muna dashi agida”. Tura baki M Jameel Yayi kana yace. “Iyeee to na haƙura tunda ba aso ayimin kyautar”. Ummi Kam murmushi take Cike da ƙaunar su, ji takeyi tamkar su duka biyu a cikinta ta rainesu ta haifesu. Sallama suka mata kana suka fice suka shiga mota Moddibo ke mazaunin Driver yayin da M Jameel ke gefen mai zaman banza kai tsaye Masallacin da suke limancin na ƙofar gidan Sarki suka nufa sunyi tafiya mai ɗan tsayi kafin suka isa lokacin da suka isa ankira sallar Isha'i suka shiga Moddibo ne yayi limanci suka idar da Isha'i kana sukayi Asham bayan an watse kana suka fito suka shiga mota wannan karon M Jameel ke driving Kai tsaye gidan Innayi suka wuce. Ƙarfe takwas da rabi suka isa gidan bayan sunyi parking sun fito kai tsaye sashen Innayi suka shiga bakinsu ɗauke da sallama a farfajiyar gidan suka tarar da Innayi da Asma'u zaune Innayi dake gashin nama akan mangal da tarin gawayi agefenta ta daga kanta tare da Kallonsu kana ta amsa Sallamar su. Ƙara sawa kusa da ita sukayi M Jameel yaja kujera ya Zauna kana ya Kalli Innayi tare da cewa. “Innayi ya dai mai ake gasa wasa ne?”. Murmushi Innayi tayi kana tace. “Nama nake dan gasawa nasanku da cin nama kamar kuraye!”. Dariya M Jameel Yayi kana yace. “Aikam Innayi kin kyauta gashi asalin gashi na gargajiya kike yi”. Kai ta gyaɗa tana ɗaukar Plate tace. “Eh ai nasanku”. Ta ida maganar tare da miƙa musu naman data yayyanka ta zuba a Plate tare dasa musu yaji agefe sannan ta yaryara ɗa musu man shanu. Kallon Asma'u dake yi musu sannu da zuwa tayi kana tace. “Asms'u ɗauko musu capet su zauna”. Cikin murza kai gefen dama da hagu Modibbo yace. “Uhmm Innayi kin dai sanshi shi J ɗinki da son nama kamar kura”. Murmushi M Jameel yayi dan yasan tabbas Modibbo bai cika damuwa da namaba, asalima in dai gasheshene ko soyayya in dai yaci yanka huɗu zuwa biyar zaice muƙa-muƙinsa sun gaji da taunawa, in kuma dafaffene wani lokaci da haƙorin gaba zai ɗan tattauna in yaji ya gaji sai ya tura masa naman gabansa. Shi kuwa M Jameel Allah ya sani yana masifar son nama, shi kuwa Moddibo yafi bawa ƴaƴan itatuwa mahimmanci. Cikin murmushin yace. “Yoh in ban so namaba me zanso A.J Namafa shine maƙurar daɗi”. “A wurinka ba, gashi kuma kana son koyamin”. Cewar Moddibon, Asma'u kuwa ganin Innayi na kallonta cikin mamakin tace. “A'a Asma'u ɗauko musu abin zama mana”. Kai Asma'u ta gyaɗa kana ta miƙe ta shiga falon ta ɗauko capet ɗin ta shimfiɗa musu awajen da yake agyare tass babu alamar ƙazanta. Zama sukayi akai, Innayi ta sake kallon Asma'u tare da cewa. “Haɗa musu Tea sannan kisa musu zuma yaji”. Kai Asma'u ta gyaɗa kana ta miƙe ta zuba musu shayi tare da zuba wadataccen zuma aciki ta kawo musu. M Jameel kuwa Anutse ya kai yankan naman bakinsa lokaci ɗaya ya lumshe idanunsa tare da buɗe su akan Innayi kana yace. “Kai gaskiya gashin nan yayi daɗi sosai”. Murmushi Innayi tayi tare da kallon Moddibo dake cin naman kamar ko yaushe kamar dai dole, yana ɗan taunawa kaɗan-kaɗan cikin kula tace. “Kai kuma fa Moddibo?”. Ɗago kansa yayi ya kalleta kana yace. “Uhm yayi”. Girgiza kai tayi kana tace. “Wato kai dai baza ka iya Yabawa ba kenan?”. Kansa ya sake ɗagowa tare da kallonta kana yace. “Ai gashinan J ya yaba kuma danɗanon harshen mu ɗaya ne ai”. Murmushi M Jameel da Asma'u sukayi. Innayi kuwa baki ta taɓe M Jameel da Moddibo suka cigaba daci Ahankali Moddibo ya ɗago hannunsa tare da kallon tsadedden agogonsa kana ya mayar da Kallonsa kan M Jameel tare da cewa. “Sai munyi sauri lokaci ya kusa J”. Kai M Jameel ya gyaɗa tare da cire hannunsa a Plate din kana yace. “Toh shikenan mu tafi”. Miƙewa Moddibo yayi tare da kallon Innayi kana yace. “Bari naje na canza kaya”. Daga haka ya juya ya nufi sashen sa, shima M Jameel bayansa yabi. Moddibo nashiga Bedroom ya sauya kayansa zuwa Jallabiya Coffee color tare da ɗaura farin hirami irin na samarin larabawa kana ya feshe jikinsa da turarukansa masu daɗin ƙamshi. Anutse ya fito falo ya samu M Jameel da shima ya canza kayansa buɗe fridge M Jameel Yayi ya ɗauki goran faro mai sanyi sannan suka jera tare da Moddibo suka sauƙa. Kai tsaye sashen su Innayi suka koma batare da sun shiga farfajiyar gidan ba . “Toh Innayi mun tafi”. Cewar M Jameel Tana rufe roban yajin da suka ci nama dashi ta ajiye kana tace. “Toh Allah ya tsare muma yanzu muna bayanku”. M Jameel na gyara ɗaurin agogon dake tsintsiyar hannunsa ya kalleta kana yace. “Toh idan za kuje kuzo mu tafi mana sai mu sauƙe ku”. Girgiza kai tayi tare da cewa. “Ai akwai Napep zamu hau”. M Jameel kuwa kai ya Girgiza kana yace. “A'a ai abin baiyi ba bayan tanan muke tafiya kuma kuce zaki shiga Napep kawai kuzo mutafi”. Jinjina kai Innayi ta gyaɗa kana tace. “To bari mu tattara da sauri sai mu tafi”. “Toh”,M Jameel yace Shi kuwa Moddibo bai ce komai ba sai harɗe hannunsa da yayi aƙirji. Cikin sauri Innayi da Asma'u suka tattare wajen sannan suka sanya hijabansu kana suka rufe kichen da gidan suka fice abayan Mota suka zauna ita da Asma'u yayin da M Jameel da Moddibo ke gaba. Suna isa babban masallacin M Jameel yayi Parking Innayi da Asma'u suka fita suka nufi sashen mata su kuma suka shiga cikin masallacin daya cika sosai da al'umma. Bayan sun zauna Kamar ko yaushe M jameel ya buɗe musu da addu'o'in kana Moddibo ya gyara system ɗin sa tare da ƙara rage girms Idanunsa kana yasa lallausan tafin hannunsa ya gyara zaman microphone din dake gabansa tare dayin gyaran murya cikin sanyayyar sautin muryansa ya fara kamar haka: _“Auzubillahi Minal Shaiɗanir Rajim, Bismillahir Rahmanir Rahim. (10) Innalazina ya'akuluna, Amwalal yatama zhulman innama ya'akuluna fiy buɗunihim naraa,wasayaslauna sa'irah”._ Jama'ar dake wajen masallacin cikin sassarfa suka ƙaraso cikin masallacin dan basa so koda harafi ɗaya ne su rasa daga cikin karatun Moddibo saboda baiwar muryarsa. Moddibo kuwa sanyayyar numfashi ya fesar tare da jingina bayansa da kujeran kana ya cigaba kamar haka: _“(11)Yusikumullahu fii auladikum,Lilzikri mislu hazzil unsaynan.Fa'in kunna Nisa'a fauƙasnatayni falahunna sulusa ma tarak,Wa'in kanat wahidatan falahannisf,Wali abwayhi likulli wahidin Minhumassudusu,Mimma taraka inkana lahuu waladun,Fa'in lam yakun lahu waladu wawarisahuuu abwahu fali ummihi sulus.Fa'in kana lahu Ikhwatun fali ummihi sudus min ba'adi wasiyyatin yusi biha audayn,abaukum wa'abna ukum latadruna ayyuhum aƙrabuna lakum naf',a,Faridatan Minallah,Innalaha kana aliman hakima”._ Ya dire ayar tare da jan numfashin sa da ya riƙe. Jinjina kai M Jameel Yayi yayinda ayoyin ke ratsa sa cikin yanayin sakewa ya lumshe idanu kana yace. “Aya ta gaba”. Jinjina kai Moddibo yayi kana cikin zazzaƙan muryansa mai sanyi da ratsa jiki kana da nutsuwa ya cigaba da jan ayoyin saida ya kai aya ta Ashirin kana ya tsaya. Shi kuwa M Jameel Cike da tsantsar ƙwarewa da nutsuwa kana da sanin makaman tafsir ya fara fassara ayoyin tare da cikekken kaddima da kowa amintattun haɗisai da suka da munasaba da ayoyin harma da sababul nuzur na ayoyi, lokacin ɗaya cikin masallacin ya sake samun nutsuwa tafsirin na ratsa su. Ƙarfe goma dai-dai suka tashi tafsir ɗin mata suka fara fita ta ɓangarensu kafin maza suka fita acikin mota Asma'u da Innayi suka jira M Jameel da Moddibo goma da kwata dai-dai suka fito suka tafi. Acan ɓangaren Khausar kuwa yauma kamar kullum taje tafsiri ita kaɗai ta dawo duk da masallacin a ƙofar gidansu yake bakinta ɗauke da Sallama tashiga cikin falonsu Anutse ta cire hijabinta tare da nufar kichen inda take jiyo motsin Mommyta kasancewar yau itace da girki yasa ko tafsir bata jeba. Juyiwa Mommy tayi jin motsi abayan ta ganin Khausar yasa ta maida hankalinta kan aikinta kana tace. “Kin dawo?”. Kai Khausar ta gyaɗa tana kallon tuƙeƙken tuwon shinkafa da Mommy ke kwashe maran ƙarshe. Ahankali Khausar ta matsa kusa da Mommy kana tace. “Mommy ki bari zanyi miyar”. Kai Mommy ta gyaɗa kana tace. “Ok to Miyar zogala za kiyi”. Kai Khausar ta gyaɗa tare da ɗaukar. Da fara aikin haɗa miyar zogalen. Cikin abinda bai gaza awa ɗaya da rabi ba, duk ta haɗa ta sanya komai na buƙata kana. Ta rufe nan danan kichen ɗin ya kaure da ƙamshin miyar sauran kayan da Mommy tayi amfani dasu ta haɗa ta wanke tare da sauƙe Miyar ganin tayi tik gwanin kyau. Bayan ta gama ta buɗe miyar da yayi mugun kyau a ido ta ɗauki kular wani sashe ta zuba miya kasancewar babban gidana yasa kowa kaina nasa akeyi, na buɗa baki kuwa ki wacce a side ɗinta takeyi, mai girki zata sawa Lamiɗo, da Dadu, haka tsarin nasu yake. Shigo wa Mommy tayi fuskarta ɗauke da murmushi ta kalli yanda kichen ɗin yayi fess ga ƙamshin miyar zogalan da yaki kifi da naman dariko, kallonta ta mayar kan Khausar kana tace. “Sannu da ƙoƙari ki ɗauki na sashen Hajiya Bunayya ki kai mata”. Kai Khausar ta gyaɗa sannan ta ɗauka kular Hajiya Bunayya ta wuce Haidar Mommy ta ƙwalawa kira bayan yazo tace ya ɗauki kular sashen Gimbiya Dadu ya kaimata dan Mommy tunda ta lura da Khausar batason zuwa yasa ta rage aikanta sashen shi kuwa Haiydar daga sashen Gimbiya Dadu ya wuce sashen Hajiya Bunayya. Hajiya Bunayya dake zaune akan kujera ta faɗaɗa fara'ar fuskarta ganin Haiydar ta tsira masa idanu kana tace. “Babana kaine dama yanzu nake niyyan zuwa in yi maka albishir”. Murmushi Haidar yayi tare da zama kana yace. “Daga sashen Gimbiya Dadu nake nace bari nazo na gaishe ki”. Murmushi tayi masu cike da Ma'anoni tayi kana tace. “Insha Allah bayan sallah mashin ɗinka zai zo kaga dama tun shekara biyu baya naso saya maka Abbanka yace saika ƙara girma kuma kaga yanzu aika girma”. Jinjina kai Haidar yayi cike da tsananin farin ciki mara mistuwa ya gyara zamansa kana yace. “Nagode Ummah Allah yarabaki da sharrin maƙiya”. Murmushin gefen baki tayi kana tace. “Bana son godiyar nan Babana”. Cike da farin ciki ya miƙe ya nufi sashen su fuskarsa ɗauke da murmushi ya shiga falon zaune ya samu Mommy da Khausar. Kallonsa Mommy tayi kana tace. “Ina ka tsaya?”. Zama yayi daga gefen Khausar still. Fuskarsa da murmushi da yakasa ɓoyewa ya numfasa tare da cewa. “Mommy Machine ɗina ya Kusa isowa fa, kinga tun shekara biyu baya Umma taso siya min shine Abba ya hanata yace saina ƙara girma ai yanzu kam dai na sake girma bazai hana ba ta saya min Machine sabo mai kyau bayan sallah zai iso”. Khausar kuwa tunda ya fara magana ta tsira masa idanu saida ya kai aya ta sauƙe ajiyar zuciya mai zafi tare da furzar da iska daga bakinta kana babu walwala afuskarta ta kawar da kanta gefe tare da cewa. “Kai kuma farin ciki kake ko?”. Juyawa Haiydar yayi tare da kallon ta kana yace. “Sosai ma kuwa kema kamata yayi kije kiyi mata godiya”. Harara Khausar ta ɓalla masa. Murmushi Mommy tayi kana tace. “Rabu da ita ai ni zanje. A yanzu kam aika girma yanda kake da tsawon ƙafan nan”. Murmushi yayi tare da kallon Khausar kana yace. “Sosai ma Mommy ai yanzu na girma yanzu fa shekara kusan sha shida nake nema gashi mai shekara sha takwas ɗinma na fita koda yake sha bakwai ne da yan watanni ne ko gareta”. Jinjina kai Mommy tayi kana tace. “Ai lallai dai kam kama cika sha shida kam Allah yasa kafara hawa asa'a. Ubangiji ya tsareka da sharrin ƙarfe. Allah yatsare gabanka da bayanka!. Ubangiji ya makantar da idanun makiyan ka akanka!. Allah ya tsare ku ga duk kan abinda zai cutar da rayuwar ku! Allah ya muku katangan ƙarfe da dukkan abin da zai zama sharri acikin rayuwarku!”. Cike da jin daɗin Addu'ar ta Haiydar yayi Murmushi tare da cewa. “Ameen ya hayyu ya ƙayyum Mommy na”. Ajiyar zuciya Khausar ta sauƙe tare da kallon Mommy kana tace. “Ameen ya Allah Mommy tunda kinyi addu'a magana ta ƙare baza'a ji tsoron komai ba babu bakin uwa akansu duk kan mai sharri zaiyi ya gama babu abinda zai sameshi da izinin Ubangiji”. Murmushi Haiydar yayi tare da kallon Khausar kana yace. “Aikam Addah Khausy babu bakin uwa akaina duk kan wani mai mugun nufi zai ƙare akansa”. Murmushi Mommy tayi cike da ƙaunar ƴaƴan nata, kallon ta ta mayar kansu tare da cewa. “Ku tashi kuje kuyi bacci dan mu samu mu farka da wuri mu kaiwa Ubangiji bukatun mu”. Miƙewa sukayi tare da yiwa juyawa sai da safe kana kowa ya wuce ɗakinsa ya kwantar. Misalin ƙarfe ɗaya na dare Mommy ta farka kallon Lamiɗo daya miƙe yashiga toilet tayi sai kuma ta miƙe ahankali ta tafi side ɗinta. ɗakin Khausar tashiga tare da kunna haske. Idanunta suka sauƙa akan Khausar dake sharan bacci ƙara sawa tayi tare da bubbuga ƙafarta kana tace. “Khausar ki tashi kiyi nafilla”. Ahankali Khausar ta buɗe Idanunta cikin Muryan bacci ta kalli Mommy kana ta yunƙura ta zaune bakinta ɗauke da addu'a tace. “Toh Mommy”,Sannan ta Sauƙa ta shiga toilet. Juyawa Mommy tayi ta koma ɗakin Lamiɗo lokacin data shiga har ya fara Sallah kai tsaye toilet ta shiga ta ɗaura Al'wala bayan tayi ta fito tare da shimfiɗa Sallaya ta tada Sallah cikin nutsuwa ta keyi bayan tayi sujja tayi Subhana Rabbiyal a'ala³ kana ɗaura da du'inta. “Ya Allah kayuwa ƴata zaɓin alkhairi,Ya Allah kashirya Khausar kasata ahanya madaidaiciya Ya hayyu ya ƙayyum ka tsare mata imaninta, Ya Allah ka kare min Haiydar ɗina ya Allah katsaresa daga sharrin mai sharri ya Allah ka kare min ita ya Allah kabawa Ramadan da Raudat ilimi mai albarka da yayunsu dama dukkan ƴaƴan musulmai. Ya Allah katsare min ƴaƴana daga sharrin,Mutum, aljan da kuma ƙarfe, ya Allah katse min imanina Allah ka tsaremin zuciyoyinsu, ka tsaresu da sharrin hassada, ƙeta, munafurci, da ƙyashi ya Allah ka kare min mijina kabiya masa buƙatunsa na Alkhairi dama ɗauka cin al'ummar musulmai. Bayan ta idar da nafillah ta ɗauki Alkur'ani ta shiga Muraja'a. Khausar kuwa ƙarfe biyu da rabi bacci ya riƙa fisgarta akan Sallaya ta kwanta nan da nan bacci mai nauyi yayi nasarar ɗauke ta. Can cikin baccinta ta fara wani mafarki mai cike da al'ajabi ganinta tayi. Gata nan tsaye a wani ƙaton fili. Baki ɗaya ilahirin filin ashare yake kuma , yashine malale a wurin iya ganinka sai wani irin haske mai masifar ƙyalli da ɗauke idon da ya cika wajen baki ɗaya, ahankali ta ɗaga kanta ta fuskanci gabas, da sauri ta rumtse idanunta gani wata ya fito ta gabar juyawa tayi taga yamma da sauri Still nan ya fito ta yamman sake juyawa kudu tayi still ta nan ma ya fito ahankali ta sake juyawa arewa, wani irin masifeffen karkarwa jikinta ya farayi, ganin tanan ma watan yafito duk kusurwa huɗu wata ya fito sai asannan ta lura da haskensa ne yake ɗauke mata ido. Ahankali taga wani kyakkyawan. Yaro fari ƙal agabanta yayinda gashin kansa ke kwance lib-lib, daga bayansa ta hango wani kyakkyawan mutum sai dai fuskarsa na kallon gefe hannunsa na kan yaron yana shafawa cikin wata. Sanyayyar murya yake kallon yaron kana yace da ita. “Wannan shine jininmu mahaɗinmu, wannan shine sanadin haɗayyarmu bugun zuƙatanmuuuhh”. Ya ƙarasa jan kalmar cikin wata iriyar ƙasalalliyar murya mai cike da shauƙi. Ita kuwa ƙoƙari take taga fuskar mutumin sai dai ta kasa sai iya fuskan kyankyawan yaron take iya kallo. Dai-dai lokacin kuma ta buɗe Idanunta jin Muryan Mommy nacewa. “Khausar, Khausar ki tashi zaki makara fa ƙarfe huɗu tayi bakiyi Sahur ba anjima kaɗan zaki fara ce mana kin fara jin wahalar azumi”, Ta faɗa tana buga ƙafarta da saurin Khausar ta tashi zaune tare da sakin ajiyar zuciya kana tace. “Innslillahi wa'inna ilahi rajiu'n Hasbunallahu wani'imal wakin Astagfirullah wa'atubu ilaik”. Sai kuma tayi addu'a ta shafa. Mommy dake tsaye har yanzu kuwa sake taɓata tayu tare da cewa. “Khausar kada ki koma bacci fa kitaso”. Kai ta gyaɗa kana tace. “Mommy na tashi bazan koma ba”. Juyawa Mommy tayi ta fice ita kuma Khausar toilet ta shiga. Brush tayi kana ta fito kai tsaye falon ta nufa. Samu tayi Mommy ta haɗa mata ɗumamen tuwon jiya da Tea mai kauri ahankali ta zauna tare da kai tuwon bakinta da ƙyar ta haɗiye baki ɗaya jikinta yayi mugun sanyi da mafarkin da tayi. Mommy dake zaune a kujeran falon ta juya ta kalleta ganin bata cin tuwon yasa ta girgiza kai tare da cewa. “Kici abinci fa Khausar kin sanki sarai da cin abinci anjima kaɗan zaki fara cewa yunwa kike ji”. Ajiyar zuciya ta sauƙe tare da fesar da iskar bakinta kallon Mommy tayi kana cikin sanyin murya ta lumshe Idanunta tare da cewa. “Mommy wallahi tuwon ne nakeji kamar ba zai shiga ba babu wani abu ne?”. Kai Mommy data tsira mata Idanu ta gyaɗa kana tace. “Kije kichen akwai indomie dana ɗaura wa Haiydar shima yace ba zai ci tuwo ba to amma ke kam nasan indomie ba wani riƙe Miki ciki yake yi ba”. Lumshe Idanunta tayi kana ta buɗe su akan Mommy ahankali ta motsa laɓɓanta tare da cewa. “Bari in cisa yau ɗin kam amma Mommy da kifi ne koda nama”. Tayi tambayar ne domin bata fiye son kifi ba. Kawar da kai gefe Mommy tayi kana tace. “Da kifi ne idan zaki ci kici idan kuma baza kici ba ki bari”. Ajiyar zuciya ta sauƙe tare da jan siririn tsaki kana tace. “Bari dai inci, tuwon ne naji kamar bazai ciwu ba shi ɗin ma miyar aida kifi”. Mommy dai Bata sake cewa komai ba ahankali Khausar ta miƙe tashiga kichen ta ɗauki Plate ta ɗibi yanda zai isheta kana ta fito ta zauna tare da Bismillah ta fara ci bayan ta gama ta ɗauki tea da Mommy ta haɗa mata da bread taci. Haiydar ne ya shigo da Sallama idanunsa akan Plate da Khausar ta gama cin indomie. Kallonsa Mommy tayi kana tace. “Jeka ɗebo indomie yayi sannan ka taho min da tuwo”. “Toh",Ya amsa kana ya wuce kichen ɗin ya juye indomie sannan ya zubawa Mommy tuwon ya fito. Khausar dai na zaune tana lumshe Idanunta tare da tuna irin mafarkin da tayi wanda ya tuno mata wanda tayi shekaru biyu baya a Jauro Yayah. Ahankali ta saki ajiyar zuciya tare da juyawa ta kalli Haiydar da yagama Sahur ɗin ta gyara zamanta tare da cewa. “Haiydar nikam yanzu wani surah kake?”. Murmushi yayi kana yace. “Ke ɗin wace surah kike?”. Zama ta gyara tare da cewa. “Hmmm aini nayi nisa ina Maryam kaga insha Allah zan samu sauƙa biyu”. Kai ya gyaɗa mata tare da cewa. “Toh ni ina Yasin Insha Allah zan samu sauƙa uku insha Allah duk azumi goma zanyi sauƙa ɗaya”. Murmushi Mommy dake duba wani littafin addini tayi kana tace. “Masha Allah yayi kyau Khausar ya akayi kika tsaya wasa ya wuce ki”. Langwaɓar da kai tayi kana tace. “Mommy kinga ai shi baya taya ki yin aiki nice ke tayaki aiki kinga shi duk lokacin daya keso zaiyi karatu. Jinjina kai Mommy tayi kana tace. “Eh haka ne da wannan dan wannan amma dai ki dage kema”. Kai ta gyaɗa kana tace. “Toh shikenan Mommy zan dage insha Allah amma Mommy ke izu nawa kikayi”. Murmushi Mommy tayi kana tace. “Insha Allah nima zan samu uku kaman na Haiydar”. Ware Ido Khausar tayi tare da tura madedecin bakinta kana tace. “Insha Allah nima zan dage duk azumi goma sai nayi sauƙa”. Jinjina kai Mommy tayi tare da faɗin. “Aikam da kin kyauta amma sai kin rage baccin safe”. Jinjina kai Khausar tayi kana tace. “Insha Allah zan rage”. Jin kiran assalatu yasa suka miƙe Haiydar ya tafi masallaci Mommy da Khausar suka shiga ɗaki suka ɗaura alwala kana suka gabatar da sallah bayan sun idar Khausar ta zauna tayi Azkharul sabah tana gamawa ta mike ta dawo falo ta gyara tare da sharewa kana ta fita zuwa kofar sashen nasu ta gama share ko ina sannan ta wuce Bedroom ta kwanta kasancewar akwai mai yi musu wanke-wanke tun kafin su shiga Sallah ta zo ta kwashe kayan ta wanke. Ahankali azumi ya cigaba da tafiya kwanaki suna tafiya lokaci yana ja cikin ikon Allah har angama goman farko goma na marmari inji hausawa ko?. Har an shiga goma na biyu, goma na wuya ko? Yau an kai azumi na goma sha biyu. Yayin da Aɓangaren Moddibo da M Jameel sunyi nisa acikin tafsirin Suratul Nisa sun fassara har zuwa ayoyi na tamanin da tara zasu tashi akan aya na Casa'in Da daddare Misalin ƙarfe tara M Jameel da Moddibo ne zaune acikin masallaci gaban ko wannensu ɗauke da system da kuma roban Swan water mai sanyi Moddibo na cikin shigarsa as Usual kamar ko yaushe Jallabiya Neavy blue kansa ɗaure da Hirami M Jameel kuwa sanye yake cikin gezner blue da babbar riga. Cike da nutsuwa M Jameel Yayi gyaran murya tare da hura Microphone ɗin kana yace. Ya buɗe da addu'a kamar ko yaushe. Lokaci guda masallacin ya kaure da kabbara tamkar zasu tsaga masallacin saboda yanayin zafin jinjinsa da kwarjininsa cike da sakin fuska. Ya cigaba da cewa. “Anma ba'ad faya Ikhwatul musulmi Assalamu alaikum warahmatullah wabarkatuhu”. Atare suka hada baki wajen cewa. “Wa'alaikum Salam warahmatullah wabarkatuhu”. A hankali ya numfasa tare da sauƙe nan-nauyan ajiyar zuciya kana ya dubi ɗumbin jama'ar dake zaune acikin masallacin cikin tsantsar nutsuwa ya juyo da system ɗin gabansa kana yace. “Acigaba da tafsirin Alkur'ani mai girma Amasallacin. Juma'a dake ƙofar gidan Mai martaba Sarki Gembulan Lamido Bashiru zamu cigaba da tafsirin Alkur'ani mai girma acikin Suratul Nisa'i zamu tashi a aya ta cassa'in”. Sai kuma ya juya ya Kalli Moddibo kana yace. “Aramma Bismillah”. Jinjina kai Moddibo yayi tare da gyara zamansa kana ya ɗan jingina bayansa da jikin kujeran cikin Sanyayyar muryarsa mai cike da nutsuwa da zaƙi yayi basmala kaya ya fara karanta ayoyin kamar haka; _“(90)Illallazina Yasiluna Ilaƙaumim Bayna Kum wa Bayna hum misaƙun Auja,Ukum hasirat suduruhu an yuƙatalalukum.Walau sha Allahu lasallaɗhum Alaikum falaƙatalukum.Fa'in'itazalukum falam yuƙatilukum Wa'alƙau Ilaikumussalama fama ja'alallahu lakum Alaihim Sabila”._ Moddibo ya ida kai Ayar yana mai lumshe idanunsa akuma take tsikar jikinsa suka tashi yayi saurin buɗe idanunsa tare da ƙoƙarin dai-dai-ta nutsuwarsa kana ya cigaba da furta Aya ta gaba kamar haka. _“(91)Satajidunah Akharina Yuriduna Anyamanukum Wayamanu Ƙaumahum kullamaraduu Ilalfitnatin Urkisu fiha.Fa'in lam ya'atazilukum Wayulƙau Ilaikumussalama Wayakfuru Aydiyahum Fahuzuhum Waƙtuluhum haysu saƙiftumuhum.Wa Ula'ikum ja'alnalakum Alaihim sulɗanammubina”._ Wani irin numfashi M Jameel ya saki tare da rintse idanunsa kana jikinsa ya ɗauki tsuma yana mai jin fassarar Ayar na yawo Atsakiyar kansa Atake kuma zuciyarsa ta cigaba da bugawa da kaso tamanin cikin ɗari. Yayinda gaba ɗaya al'ummar dake cikin masallacin dama wajensa sit kakeji kamar ba mai numfashi sabida tsananin yadda sautin karatun ke ratsa musu zuƙata da ƙoƙwale. Shi kuwa Moddibo ya kai minti ɗaya kafin ya saki gauron numfashi gaba ɗaya jikinsa yayi sanyi sabida sanin ma'anar ayoyin da zai kawo a gaba, cikin wani irin raunin tare da tsoron Allahu wahidun ƙahhar, gaba ɗaya muryarsa ta sake rauni cikin dakiya ya cigaba da Karanta Ayar Kamar haka. _“(92)Wama kana limu'uminun An yaƙtula Mu'uminan Illakhaɗa'a.Waman ƙatala Mu'uminan khaɗa'a fatahriru Raƙbatatin Mu'uminatin wadiyyatun Musallamatu Ila'ahlihee Illah An yassaddaƙun.Fa'in kana min ƙaumin Aduwwillakum Wahuwa Mu'uminun Fatahriru Raƙbatin Mu'uminatan.Wa'in kana min ƙaumim baynakum wa baynahum miysaƙun Fadiyyatun Musallamatun Ila Ahlihi watahriru raƙbatin mu'uminatin.Famallam yajidu fasiyamu shahraini mutatabi'ayni taubatan Minallah.Wakanallahu Aliman hakima”._ Wani irin nutsuwa cikin masallacin yayi musamman ma wa'anda suka san fassarar ayoyin wa'anda basu san fassarar ba kuwa mu'ujiza ta Kur'ani ta dinga ratsasu tare da Sanyayyar sautin Muryar mai karatun. Moddibo kuwa idanunsa ya lumshe sakamakon wasu zafafan hawaye masu ɗumi da suka cika cikin ƙarfi ya furzar da iska mai zafin gaske Tabbas kashe ran mumini baƙaramin tashin hankali bane amma baki ɗaya awannan zamanin an maida rai ba abakin komai ba. Ya gyara zamansa tare da cigaba da karantar Ayar kamar haka. _“(93)Waman yaƙtul mu'uminan Muta'ammidan Fajaza's'uhu Jahannama! halidan fiha wagadiballahu Alaihi wala'anahu! wa'aaddalahu Azaban! Azeeymah!!!!!”_. Awannan lokacin hawaye ne suka ciko idanun Moddibo jin irin tsananin azaban da Ubangiji ya tana darwa duk wanda ya kashe ran mumini batare da wani hakkiba. Walahabahu la'anar Ubangiji kana fajaza'ahun jahannamu khaleedan fiha, fa ubangiji yace kana aka ɗaura da Azaban Azeeymah!!!, Duk wannan tanadinefa da Ubangiji yayiwa mai kashen ran mumini da gangan. Wani irin rawa jikin Moddibo keyi tamkar wanda aka konawa wuta a jikinsa cikin tsananin sheshsheƙan kukan da yake son dannewa ne ya bu ɗe baki a hankali dan kawo aya ta 94 sai kuma ya juyo cikin tsananin rauni ya kalli M Jameel da gaba ɗaya j.... *WOHOHO IN KAJI ANA ƘI GUDU TABBAS SA GUDU NE BEZO BA* _Ina kuke Ma'aurata masu sha'awar ganin sun zama taurari kuma fitilu a idanun mazajensu Uwar gida,Amarya,Tsakar gida,hadda tan kaɗen gida Shararriya kuma ƙasaitacciya data saba kawo muku nau'ikan sirrin sahihan magungunan ma'aurata wato *AYSHA ALIYU GARKUWA* Garkuwar Marubuta ayau ma ta dawo muku da Ingantattun magungunan mata masu kyau da inganci domin gyara kanki ki zamto tauraruwa a idanun mijinki...Muna da Ingantattun Abubuwa kamar haka_ :_Munada Garin mallaka, garin maɗi, garin Hakkin mayi, garin ɓelɗamhi Garin ilanwaddihi, Gumbar da ba'a baiwa mai kishiya, Gumbar kolli mai kellin al'khairi, Gumbar Riɗi wato 3 in 1, Gumbar makwaranyi, Masin Maliƙi mai masifar ƙarfi da matse mace, ka masin Daɗi har Maɗigan Akwai, kwanon ƙasaitacciyar mace mai masifar kyau da ratsa jiki da samar da inƙantacciyar ni'ima yanada abubuwa masu kyau haɗinsa, Zumar goron tula mai masifar kyau, tsumin dabino, mai ratsa jiki, tsumin Riɗi mai ƙarfi, Furar Mata mai tsastsafo da ni'imantaccen damshi, Cida kaza, Ciccibi Abodi, Tsumin Ɓaure, tuwon ɓauren, kana akwai maganin sanyi sadidan, da dai sauransu...Se kuma fannin ƙamshi kasance da Shu'umin ƙamshi wanda ze gigita ƙwaƙwalwar Oga tare da jin ko wacce mace bata kaiba...._ _Shin ko kina da labarin Miskilinci da ƙasaitar Rayyan Naaan amma lokaci ɗaya ya zamto zautacce sakali akan soyayyar Jannart bakomai Jannart ta riƙe ba face sirrinkan gyara da kuma shu'uman humran da kulaccar sirri na Aysha Aliyu Garkuwa(Tubali) tabbas taga tasirin haka domin Naanunta ya zame mata tamkar bawa_ _Shin ko kinsan sihirtaccen haɗin da Aysha ke sha kenan ta zamto tauraruwa a idanun Hamma Yusuf(Miwasmiti)...Tabbas Mahmud ya zamto zautacce kuma makaho akan sauyayyar Bazawara wato khadijarsa duk da kuwa gashi da budurwa(Namiji Baya Kaɗan) ko kinsan hakan nada alaƙa da amfani da sahihan maganin da kuma shu'uman humran Aysha Aliyu Garkuwa??.Nasan ba zaka ku manta da irin kima da kuma darajar da Aysha ke dashi acikin Idanun Sheik Jabeer ɗin ta duk da kuwa shekaru sunja anma jinta yake tamkar budurwa 'yar sha bakwai(Garkuwa) sirrin hakan na tare da Ingantattun kuma sahihan magungunan Aysha Aliyu Garkuwa Wato Garkuwar Marubuta da kuma Ma'aurata na tabbata kunsan da cewa basirarta ba'a iya rubutun littafi ya tsaya ba hadda inganta rayuwar ma'aurata ta hanyar kawo musu Nagartattun abubuwa Ga duk wacce ta shirya saya seta tuntuɓi number ta 09097853276 muna iya tura kayan mu aduk inda kuke afaɗin Nigeria harma da ƙetare Dan Allah 'yar uwa idan baki shirya siyaba kada kiyi min magana muɓatawa kanmu lokaci...._ 🤝🏻🤝🏻🤝🏻🤝🏻🥰😘sai.kunzo. sayan na gari maida kuɗi gida, *By* *GARKUWAN MARUBUTA* [19/07, 8:57 PM] Halimatu A/rahman Sadeeya: 📝✨💫⏰🤴🏻👹❤️❤️❤️🍇 *SAKAYYAH* _page 16_ _NA_ *AYSHA ALIYU GARKUWA* 🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 *In sha Allah daga gobe zan gama free page, ƴar uwa baki makara ba ki biya ki karanta cikin Aminci littafin SAKAYYAH 1k ne kacal 0661110170 GTBank AISHA ALIYU GARKUWA sai ki turo min shaidar biyanki ta WHATSAPP 09097853276 daga wannan page ɗin sai na gobe mun gama free page, ki biya yafi sauƙi tsira ba haƙƙin kowa kanki.* *GARKUWAR* taku ce dai MA'AURATA, da masu shirin aure, da masu jego, da yan gayu masu son k’amshi kece raini, da gyaran da zaike maimaita muku dararen forkon kuruciya* Ko kunsan Jikinmu na da sinadaran hormones da suke taimakawa dan’adam akan komai musamman lokacin da mace take mu’amalar aure da mijinta. Mafi akasari wannan hormones din ne ke samun matsala ko su yi sanyi koma su daina aiki kwata-kwata shi ne dalilin da zai sa mace tace bata jin sha’awa ko bata san dadin aure ba. Albishirinku ina da kayan da ke taimakawa wannan sinadaran du dawo aiki tukuru don karkato miki da kimarki wajan mai gida sannan su taimakawa wannan sinadaran hormones dinki su dinka secreting din ni’ima wadatacciya da zata taimaka miki ki gamsu mijinki ya gamsu fiye da tunaninki. Note: Kayana ba sa tsinka ruwan ni’ima suna dai taimakawa hormones dinki ne su tsattsafo da ni’imar musamman wacca cutar sanyi ko dattin mahaifa ya dankarar da su ya hana su yin aikinsu yanda ya kamata. Haka zalika idan kina da kyau ki kara da wanka. Zaki iya amfani da magani na na gargajiya wanda zai gyara miki sex hormones din kullum ki kasance cikin humidify wato cikin damshi mai albarka kamar yanda ake son mace. Yana gyara miki mara. Sai kamshi. Hajiyata daure ki fara amfani da turarena ki ji irin salon kamshin sa salo ne da zai daidaita ki da mijinki ya kankaro miki da kimarki a wajansa. Siyan na gari mayar da kudi gida. Ga masu buƙata ga number' wayata wanda nake whatsApp dashi 09097853276 kimin mgn ta whatsApp in har kin tabbatar kin shirya saya mu dai-dai ta, kayana ba ƙanana bane, shiyasa bana harkan karanta, muddin kinsan baki shirya sayaba Please kada kiyi min mgn ki bari sai kin shirya kuɗinki a hannu, ba ina nufin kayana bana talaka bane, no akwai ƙananan set na masu karamin karfi, banson aimin mgn a ɓatamin lokacin aiyukana a shirme baki shiryaba. Shine karantan da bana so. 0005388578 Jaiz bank AISHA GARKUWA ALIYU. In kin shirya ga number ta ga kuma account number ta wanda in mun gama mgn zaki turo kudin ki, kana insa miki kaya a mota, duk ƙasar da kike kayana zaije gareki, amman fa in kinada dalilin zuwan nasune🤝🏻sayan na gari meda kudi gida. GARKUWAR MA'AURATA Shiko M Jameel Wani irin tsuma ilahirin jikinsa keyi sakamakon tuni da ayoyin sukayi mishi na jin azabar da Ubangiji ya tanadar wa da duk wanda ya kashe ran mumini da gangan ba tare da wani haƙiba. Cikin raunin murya me cike da tsananin tsoron Ubangiji M jameel ɗin ya kawo fassarar aya na 90 da kuma 91, tsit gaba ɗaya masallacin yayi babu abinda ke tashi sai sautin kukan M Jameel daya kasa ci gaba, yayinda kukansa yasa da dama cikin mutanen yin kuka. Middibo kuwa kife tafukan hannunsa yayi kan fuskarsa yana maiyin wani irin sassayan kuka mai masifar sa rawan jiki, gaba ɗaya fuskarsa tayi jazir. Cikin ƙarfin hali M Jameel ya fara mgn cikin rawan murya yace. “A cikin suratul Nisa, Aya ta 92 Allah ma ɗaukakin sarki na cewa, 92: -:Baya halasta ga mutum da ya kashe ran mumini, sai dai idan ya kasance kuskure ne.”. Sai kuma ya tsagaita tare da sayan tafin hannunsa ya share hawyen daketa kwaranyowa da idanunsa, cikin rawan murya yaci gaba da cewa. “Duk wanda kuma ya kashe! Mumini da kuskure toh, zai ƴanta wuyan Muminin, sannan ya bada Diyya ga iyalan wanda ya kashe”. Sai kuma ya dire ayar mgnar tare da rushewa da zazzafan kuka mai cike da tashin hankalin da raunata zukata aya ta 93. Cikin rauni yasa hannu ya karɓi hankicif ɗin da ɗan agajin dake bayansa ya miƙa masa, sharce hawayensa yayi tare da juyowa ya kalli Moddibo da gaba ɗaya jikinsa rawa yake sai sheshsheƙan kuka mai fuzge numfashin da yakeyi, bazai iya hana kansa kuka ba, bare ya samu iko da damar hana aminin nasa. Cikin sheshsheƙan kuka M Jameel ya gyara zamanshi tare da cewa. “Huymmmm, a kuma cikin suratul Nisa ɗin ayata 93, Allah madaukakin sarki nacewa-: (Duk wanda ya kashe Mumini bisa ganganci, ko Mugunta da zalumci. Toh Sakamakonsa shine wutar Jahannama”. Sai kuma ya sake sakin wani irin raunataccen kuka mai cike da tsoro kana yaci gaba da cewa. “Allah madaukakin sarki cewa yayi-: Duk wanda ya kashe ran mumini zai dawwamane cikin jahannama, kuma Allah yayi fushi dashi, sannan kuma ya tsine masa”. Kawai sai ya kife kansa bisa Table ɗin dake gabansa, shar-shar haka hawayensa ke kwaranyar babu ƙaƙƙautawa. Modibbo kuwa cire tafukan hannunsa yayi bisa fuskarsa tare da dafa kafaɗar M Jameel ɗin kawai saka sufashe da kuka a tare, cikin kukan murya na rawa M Jameel ya buɗe baki da nufin zaiyi mgn amman ina ya kasa. Haka yasa Moddibo rumtse idanunsa kana murya na rawa yace. “Bayan fushi da tsinuwar ubangiji Allah Mabuwayi da komai baya ɓuyar masa yace. -:Wa ahdalahun Azaban Azeeymah). Ma'ana ya tandarwa duk wanda ya kashe ran mumini da ganganci Azaba mai girma!!!!.” Zuwa lokacin wasu daga mutanen cikin masallacin kuka sukeyi da sheshsheƙan mafi akasari kuma duk jikinsu yayi sanyi. Shi kuwa Moddibo cikin rauni da sanyi yace. “Duk waɗannan ugubobin sun ta'allaƙane ga wanda ya kashe ran mumini da ganganci, sakamakonshi Jahannama, kuma a cikinta zai tabbata, sannan Allah yayi fushi dashi, kana ya tsine masa, kuma ya ƙara masa da azaba mai girma. Wannan masifa har ina ɗan adam zai kaishi koda iyayenka ne sukayi fushi da kai taɓewa kakeyi bare Ubangijin talikai, koda iyayenka ne suka tsine maka lalacewa kakeyi bare tsinuwar Allah, sannan azaba koda ta tururin tea ne tsoronsa muke bare kuma tabbata ta jahannama sannan da tanadin azaba mai girma”. Kawai sai lips inshi suka fara rawa kar-kar shima ɗin ya kasa ci gaba. Ganin hakane yasa M Jameel sharce hawayensa tare da cewa. “Aramma kawo mana dukkan wata Ayar Al,qura'ani da Ubangiji yayi magana akan duk wanda ya kashe ran mumini”. Cikin tsumar jiki tare da wata raunatacciyar murya mai cike da tsananin tsoron Ubangiji da kuma sanin hukuncin wanda ya saɓa masa Moddibo yayi gyaran murya dai-dai zai fara karanta Ayar manyan Malaman dake wajen suka nuna musu agogon dake liƙe a can bayansu a jikin gini. Wanda hakan ke musu nuni da alamar lokaci yayi. Nan-nauyan ajiyar zuciya M Jameel ya sauƙe tare da share ƙwallan da suka zuba masa kana cikin raunin murya yace. “Lokaci yayi sai dai idan Allah ya kaimu gobe zamu ɗaura daga inda muka tsaya”. Ya sauƙe nannuyar Ajiyar zuciya tare da cewa. “Ya Allah Ubangiji yabamu zaman lafiya ya Allah karabamu da sharrin ƴan bindiga daɗi Ubangiji ya tsare mu da sharrin kidnappers Ubangiji ya bamu zaman lafiya Allah yajiƙan iyayen mu da duk kan musulman da suka rigamu gidan gaskiya. Wa subhanakallahumma wabi hamdika ash shahadula'ilahu. nastagfirka wanatuubu Ilaik”. Tunda ya fara addu'ar suke Amsawa da Ameeen har aka shafa. Mata ne suka fara fita kafin maza. Acan ɓangaren Khausar kuwa, bayan ta koma gida kai tsaye Bedroom ɗinta ta wuce batare data shiga wajen Mommy ba, tana shiga ta kwanta lamo akan gado hawaye na tsiyaya daga kyawawan Idanunta sosai. Tafseer ɗin da M Jameel Yayi ya riƙa ratsa jikinta har ƙwaƙwalwar kanta Muryar Modibbo kuwa har yanzu yana ratsa kunnuwanta, da haka bacci ya ɗauketa batare data shirya ba. Washe gari Da safe still haka Khausar ta tashi cikin mutuwar jiki Anutse ta fito daga Bedroom ɗin ta zauna agefen Mommy dake falo. Lumshe Idanunta tayi kana cikin sanyin murya tace. “Mommy ina kwana”. Anutse Mommy ta maida kallonta gareta tare da na zartan yanayin ta batare data amsa gaisuwar data mata ba ta jefo mata tambya tare da cewa. “Meke damunki Khausar na lura tun jiya jikin ki Asanyaye”. Ɗago Kai Khausar tayi Idanunta cike da ruwan hawaye kana cikin sanyi murya tace. “Wallahi Mommy tun jiya da muka je wajen tafsir ɗin da Malam M Jameel yayi jikina ya mutu hankalina ya tashi gaba ɗaya na rasa mai yasa tsoro ya kamani”. Miƙewa Mommy tayi tare da matsowa kusa da Khausar ta shafa kanta kana tace. “Babu komai wannan masiface-masiface ne da Allah ya jarabci Al'umma wannan ƙarnin saidai mu dage da addu'a Allah ya yaye mana ya kuma tsaremu da faɗa wa mummunar ƙaddara Allah ya rufa mana asiri ya karemu da zamewa sanadin mutuwar koda kadagare ne”. Jinjina kai Khausar tayi tare da cewa. “Ameen”. Acan gidansu Moddibo kuwa Innayi ce zaune atsakar gida ta zabga tagumin tunda taji tafsirin da M Jameel sukayi jikinta yayi masifar sanyi wani irin tsoron Allah mara misaltuwa tashiga hakan fargaba ya rufeta. Washe gari. Da hantsi A hankali Moddibo da M Jameel suka fito, Moddibo na sanye cikin Shigarsa as Usual Jallabiya Sky blue mai yauƙi da santsi kansa ɗaure da farin Hirami kana takalmamsa farare jikinsa na fitar da sanyayyan ƙamshi turaren Oud Khareem na tashi. Shima M Jameel sanye yake cikin irin shigar Modibbo jikinsa na fitar da sanyayyan ƙamshi kai tsaye sashen Innayi suka nufa,Innayi dake zaune gaban barandar akan kujera ƴar tsugunno ta ɗago kai ta kalli Moddibo da M Jameel kawai sai taji Idanunta na tsats-tsafowa da ruwan hawaye. Tsayuwa Moddibo ya gyara kana yace. “Ya dai Innayi”. Idanu ta zuba masa batare data iya furta komaiba kawai sai hawaye suka shiga kwaranya daga idanunta. Cikin yanayin tashin hankali Moddibo ya tsugunna agefenta na dama yayin da M Jameel ya durƙusa agefenta na hagu kana suka haɗa baki tare da cewa. “Innayi ya dai me yasame ki?”. Kallonsu tayi hawaye na cigaba da kwaranya daga idanunta ta sauƙe numfashi kana tace. “Wa'azinku na jiya ya ratsa jikin mutane wa'azin yasa mutane acikin ɗimuwa wa'azinku na jiya ya tunatar sannan yasa tashin hankali kuma wannan zamanin muna fama da Masifa Allah dai ya yaye mana jiya hankalina atashe yake domin ire-iren abubuwan akeyi!”. Jinjina kai M Jameel yayi tare da sauƙe numfashi kana yace. “Hakane sosai ma Innayi amma mu cigaba da addu'a babu abinda ya gagari Ubangiji ga dama yazo watan Ramadan muyita addu'a Allah ya yaye ya taƙaita ya sauƙaƙa mana”. Atare Modibbo da Innayi suka amsa da. “Ameeen”. Miƙewa M Jameel da Moddibo suka atare kana M Jameel ya Kalli Innayi tare da cewa. “Toh Innayi zamu tafi Tafseer A masallacin makarantar mu”. Jinjina kai Innayi tayi kana tace. “Ubangiji Allah ya tsare ku ya kuma sake ɗaukaku”. Ameeen suka amsa tare da juyawa zasu fita har sun kai ƙofa Innayi ta ɗan ɗaga sautin Muryanta tare da cewa. “Yauwa wai niko ya batun tafiyar mu ne?”. M Jameel ya juya tare da cewa. “Komai ya kammala na tafiyar mu Insha Allah ranan sha biyar ga wata zamu tashi misalin sha biyu da rabi na dare jirginmu zai tashi jibi kenan ba in sha Allah, kuma sai munyi tafsir ɗin ranan ma zamu tafi Taraba”. Kai ta gyaɗa kana tace. “Allah ya nuna mana Ubangiji Allah ya kaimu lokacin lafiya amman kuma kace sai kunyi tafsirin ranar?”. Kai ya jinjina tare da cewa. “Eh kinga Tara na dare zamu fara, goma zamu tashi, dama kuma kafin mu tafi zamu gama shirin mu duka, tsananin mu Gembulan da taraba kuma tafiyar awa ɗaya da rabine, kinga kenan sha ɗaya da rabi zamu isa, zamu samu awa ɗaya ma acan kafin mu tafi, Abba na kuma su gobe nema zasu tashi”. Cike da gamsuwa Innayi ta jinjina kai tare da amsawa. “Allah ya kaimu lfy”. Ameeen suka amsa a tare kana suka fice mota suka shiga M Jameel ke Driving cikin nutsuwa har suka isa masallacin. Suna shiga suka fars gabatar da tafsirin kamar yanda suka saba ƙarfe ɗaya da rabi dai-dai suka gabatar da sallah Moddibo yayi limanci bayan sun idar suka cigaba kiran sallar La'asar yasa suka dakata da karatun tare da miƙewa suka gabatar da sallah bayan sun idar suka fito suka shiga mota awannan lokacin ma M Jameel ke Driving har suka iso gida. Hong M Jameel Yayi Modibbo ne ya fita ya buɗe musu. Anutse suka fito tare da furta Bismillahi, Ahankali Moddibo ya gyara tsayuwarsa tare da fesar da sassayan numfashi. Ido ya tsirawa bishiyar Ayaba da iska ke kaɗawa har na tsawon sakonni goma, sai kuma ya maida kallonsa kan Bishiyar mangoro Idanunsa ya lumshe domin Allah ya sani ganin sirrai ya fiye mishi ganin komai daɗi. sannu ahankali ya riƙa tuna lokacin da yarinyar tashigo gidan har tayi nasaran hawa reshen bishiyar mangoro mai girma da tsawo, da kuma sanda ta faɗo akan yatsun ƙafarsa. Da sauri ya buɗe idanunsa Tare da jan dogon tsaki mai cike da tsanar lamuran yarinyar. Idanunsa ya juya jin M Jameel na cewa. “A.J tunanin mai kakeyi haka ka tsiwara Bishiya ido?”. Sanyayyar Ajiyar zuciya Moddibo ya sauƙe tare da furzar da iska mai sanyi daga bakinsa kana yasa hannu ya shafa kwantaccen Sajen fuskarsa ya maida kallonsa kan M Jameel da har zuwa lokacin shiyake kallo,Ya mutse fuska yayi kana yace. “Babu komai”. Daga haka ya wuce gaba Kai M Jameel ya Girgiza tare da bin bayansa suka shiga Babban falon Moddibo da komai ke kimtse sai tashin ƙamshi yake. Zama M Jameel Yayi akan 3sitter tare da faɗin. “Wash' Allah!”. Kallonsa Moddibo yayi amma bai ce komai ba Bedroom ya nufa tare da janye Hiramin kansa kana ya cire jallabiyar dake jikinsa ya buɗe ƙofar toilet da addu'a Kana yashiga shawer ya sakarwa kansa yashiga cuɗe jikinsa ya ɗauki kusan minti ashirin kafin ya fito zama yayi agaban Dressing mirrow ya shafa Mai sama-sama kana ya miƙe ya sanya Jallabiya Maroon colour da farin hirami. Feshe jikin sa da turarukansa masu daɗin ƙamshi yayi. shima M Jameel wanka yayi tare da sauya kan jikinsa zuwa Jallabiya fari kana ya ɗaure kansa da Maroon Hirami Sosai sukayi kyau atare suka fito zuwa farfajiyar gidan anan suka samu Innayi da Asma'u na aikin abin buɗa baki kallon Innayi dake soya ƙosai yayi sai kuma ya maida kallonsa kan Asma'u dake dama kunun sadaka na masallaci har ta gama ta rufe sai kuma suka bita da ido. Kallon Asma'u dake kwaɓa fulawa, kuka, da kanwa M Jameel Yayi yace. “Yau kuma ɗan wake ake mana ne Asmeey?”. Kai ta jinjina kana tace. “Eh dan naji jiya Yaya Moddibo nacewa ɗan wake mukayi ne shiyasa yau nace bari ayi”. Murmushi Moddibo yayi ya mai binta da wani irin amintaccen yace. “Kai kin kyauta mun kuwa, kwana biyu bamuci ba inaga tunda azumi ya kama kamar baku yimana shiba”. Kallonsa Asma'u tare da ce wa. “A'a munyi amma ranan baka ciba agidan Ummi kuka sha ruwa ranan”. Jinjina kai yayi yace. “Toh yau kam Insha Allah zamu dawo muci ɗanwaken nan”. Murmushi tayi ta na jefa ɗan waken da cokali tace. “Allah ya dawo daku lafiya”. Ameeen suka amsa kana suka mayar da Kallonsu kan Innayi dake musu gashin Zabbi sai tashin ƙamshi yake. Idanu M Jameel ya lumshe yace. “Innayi zamu wuce”. Da murmushi afuskarta ta kallesu tace. “Ubangiji Allah ya tsare”. “Ameen”,Suka amsa sannan suka fice atare kai tsaye masallacin Juma'ar da suke limancin suka nufa cike da nutsuwa da kuma kamala suka gabatar da tafsirin Alkur'ani acikin Suratul Zariyat yayin da Moddibo ke jan baƙi M Jameel na tafsiri ƙarfe shida dai-dai suka tashi. Anutse suka fito daga cikin masallacin suka shiga mota akuma dai-dai lokacin wayar M Jameel ya hau ruri cike da nutsuwa ya gyara zamansa tare da ciro wayar daga aljihun sa Sunan Abban sa ke yawo a screen ɗin kallon Moddibo da idanunsa ke lumshe yayi yace. “Kaga Abba ke kira”. Ya ƙara sa maganar tare da Amsa kiran yakai kunnensa tare da cewa. “Assalamu Alaikum”. Daga ɓangare Abba yace. “Wa'alaikum Salam Babana”. M Jameel Yayi murmushi tare da cewa. “Na'am Abba na”. Gyaran murya Abba yayi kana yace. “Nikam laifin me mukayu mukune da kai da Moddibo da baza kuzo mu samu ladan baku buɗa baki agidan nan ba”. Murmushi M Jameel Yayi yace. “Ayyah Abba na laifin me zaku mana mukam a duniyar nan gama A.J ɗin yana jinka”. Ɗan Matsawa kusa da M Jameel ɗin Moddibo yayi kana yace. “Abbah mai zaku mana A duniya ko kun yi mana abu baza muyi fushi da kuba waye zaiyi fushi da iyayensa?”. Murmushi Abba yayi yace. “Toh tun da akayi azumi baku zo kunsha ruwa a gidan nan bafa, abin yana damuna yau fa kwana goma sha uku kenan da baku zo kunsha ruwa agidan nan ba fa”. Dariya M Jameel Yayi yace. “Abba ka dai manta mun zo ranan da akayi azumi biyar agidan muka sha ruwa fa”. Gyara zaman wayar Abba yayi akunnensa kana yace. “To ai bana nan ba asha ruwan dani ba yau dai so nake kuzo musha ruwa tare”. Gyara zama Moddibo yayi yace. “Abba baza mu bari sai gobe ba?”. “A'a yau nakeson ganinku kuzo musha ruwa anan”. Cewar Abba. Jingina kai Moddibo yayi tare da lumshe idanunsa kana yace. “Toh shikenan Abba zamu zo insha Allah amma bari mu fara zuwa gida”. Cikin sauri Abba ya Girgiza kai tare da cewa. “A'a karfa ku makara kuzo komai ya kammala ku kawai ake jira ga kun lokacin ya ƙarato”. Atare suka haɗa baki wajen cewa. “Toh shikenan Abba ga munan zuwa”. Kallon Moddibo M Jameel dake Driving Yayi kana yace. “Muje?”. Moddibo kuwa Idanunsa dake lunshe ya buɗe yace. “Eh muje mana J”. Kai M Jameel ya gyaɗa kana ya juya akalar motar zuwa Unguwar su Abba ba abinda ke tashi acikin motar face ƙira'ar Alkur'ani acikin Suratu Yusuf tare da Sanyayyar ƙamshin tularensu, Wayar Moddibo dake gaban aljihu ne ya hau ruri Anutse yasanya lallausan tafin hannunsa mai zagaye da gashi ya ciro wayar tare da kallon sunan mai Kiran Malam Arɗo amsa kiran yayi tare da kai wa kunnensa. Daga ɗaya ɓangaren Malam Arɗo yayi gyaran murya kana yace. “Wai kai baza kazo kasha ruwa agidana ba ko sau ɗaya ne Moddibo?”. Murmushin gefen baki Moddibo yayi tare da shafa kwantaccen Sajensa kana yace. “To Malam ka gayyace mune ai baka gayyace mu shan ruwa ba”. Da sauri Malam Arɗo yace. “To na gayyace ku xo yanzu”. Girgiza kai Moddibo yayi tare da lumshe idanunsa kana yace. “Toh ba yau ba dai sai gobe”. Da sauri Malam Arɗo ya zare Ido tare da cewa. “To duk abubuwan da nasa aka dafa muku kuma fa?”. Murmushin gefen baki Moddibo ya kuma yana imagine fuskarta malam Arɗo kana yace. “Ka bawa mutanen gida suci ba rabon mu bane gobe kuma Idan Allah ya kaimu kama na namu kuma ayi da mutanen gida duka”. Cikin sauri Malam Arɗo yace. “Wato dai kai ko yaushe sai ka kawo min sabon tsari acikin al'amari na ko”. Murmushi M Jameel yayi shaƙuwar dake tsakanin Moddibo da malam Arɗo ya wuce zaton mutane. Moddibo kuwa ɗan Murmushin dake ƙarawa fuskarsa kyau yayi kana yace. “Ai dole dai kam”. Dariya Malam Arɗo yayi yace. “Dama gobe ka tabbatar lokacin shan ruwa yana yi na ganka, ba sai na kira ba ka gaishe da Jamilu kar ku cinye min kati na”. Ya ida maganar tare da katse kiran. Murmushi M Jameel Yayi kana yace. “Malam Arɗo ko?”. Murmushi kawai Moddibo yayi yana motsa laɓɓansa alamar tasbihi yake. Cikin mintunan da baza su gaza biyar ba suka isa ƙofar katafaren gidan Hong M Jameel Yayi mai gadi ya buɗe musu Anutse M Jameel ya cinna hancin motarsa gidan tare da yin parking a inda aka tana da danyi Parking ɗin motoci. Cike da nutsuwa suka nufi sashen Abban M Jameel, bakinsu ɗauke da Sallama suka shiga tamfatsetsen Falon nasa daya gaji da tsawuwa yana fitar da sanyayyan ƙamshi. Tsaye suka hangosa yana gyara ɗaurin agogon hannunsa fuskarsa da damshi da alama Al,wala yayi. Kallonsu yayi tare da sakar musu da murmushi kana yace. “Ku shiga kuyi al,wala kunga muna shan ruwa sai mutafi masallaci”. Kai suka gyaɗa sannan M Jameel ya nufi toilet dake Falon kana ya kalli Moddibo da faɗin. “A.J kashi ga toilet ɗin ciki kayi al,wala”. Girgiza kai Moddibo yayi kana yace. “A'a kashiga na ciki ni zan shiga wannan”. Kallon Moddibo Abba yayi kana yace. “Wato shi yashiga ɗaki na kai ba zaka shiga ba ko? To ai kaima ɗana ne kashiga babu komai Moddibo”. Kai Moddibo ya gyaɗa kana yace. “Toh shikenan Abba”. Sannan ya wuce Bedroom ɗin Abba ahankali ya saki murmushi ganin komai na Bedroom din tsaf-tsaf akimtse Aransa yace ashe de J gadon tsafta yayi awajen Abba shima komai nashi tsaf-tsaf ajiyar zuciya ya sauƙe tare da shiga toilet ɗin nan ma komai atsaftace Al'wala ya ɗaura kana ya fito atsaye ya samu M Jameel da Abba Kallonsu Abba yayi kana yace. “Ku ƙaraso mu isa dining”. Kai suka gyaɗa tare da nufar dindin ɗin da aka ƙawata da kayan ciye-ciye na alfarma wani irin kwando ne na kayan marmari ne kama daga, Inabi, Abarba, Ayaba, Kankana, Lemo, Ruman, Tuffa, Mangoro. Sai kuma wasu Warmers masu kyau dake ɗauke da pride rice da yaji kayan lambu,sai daga ɗaya gefen kuma wasu jug ne masu kyau ɗaya kindirmo ne mai sanyi adame ɗayan kuma kunun shinkafa ne sai Flaks dake ɗauke da ruwan tea da kuma kofina daga gefensa kuma gongomin madara ne dana Bounvita sai kulan ƙosai sosai dining din ya ƙawatu. Anutse suka zauna akan kujeran Abba ya zauna daga ɓarin kudu Moddibo ya zauna daga ɓarin yamma yana fuskantar gabar M Jameel kuwa daga ɓarin gabas ya zauna yana fuskantar yamma. Anutse Moddibo ya ɗauki dabino guda bakwai ahannunsu idan yaci sai ya sanya ƙwallon ahannunsu na hagu bayan yaci sai ya ɗauki inabi yaci M Jameel kuwa dabino uku yaci tare da apple haka ma Abba. Sai.kuma suka sha kankana da inabi kana suka ɗan ɗaura da ayaba. Kallon su Abba yayi cike da so da ƙaunarsu kana yace. “Toh kuci abinci”. Girgiza masa kai sukayi kana atare suka ce. “A'a Abba sai mun dawo daga masallaci”. Kai ya gyaɗa musu kana suka miƙe atare suka tafi masallaci suka idar da sallah bayan sun dawo M Jameek ya ɗebi Pride rice Kaɗan da tsokokin kaza. Modibbo kuwa kindirmon da aka dama ya ɗiba a Cup Abba kuwa chicken peper da pride rice shima ya ɗebi yana ci. Fara cinsu babu daɗewa aka turo ƙofar aka shigo Idanun Hajiya Karima bai sauƙa ko ina ba sai kan Moddibo dake riƙe da kofin kindirmon kana da plate ɗin da Abba ya sa mishi pepper chicken and vegetables da fork a samansu. Cike da tsanarsa ta watsa masa wani wulaƙantaccen kallo kana tace. “Toh acire tsatsan haƙori anan, kaska raɓi mai jini wato ko zuwa shi kaɗai ya samu ya keɓe da mahaifinsa ba za'a bari ya samu damar hakan ba ko? Oh ni Kareeme tunda nake a duniya ni dai ban taɓa ganin mutum mai shegen nacin tsiya irin kaba, sam baka da godiyar Allah ba zaka tsaya amatsayin ka ba shin kai wani irin Jarabebben mutum ne Aliyu?!”. Cikin wani irin fushi da ɓacin rai Abba ya mike ahasale ya dubeta kana yace. “Hajiya Karima mai kikeyi haka ne? Wai meyasa ne ke baki da hankali ne? kinsan abinda kike faɗa kuwa!”. Fuska ta ɓata kana tace. “Toh Alhaji gaskiyane ya barka kaida ɗan ka kuhuta mana kuyi shawara acikin sirri”. Afusace Abba ya katseta tare da faɗin. “Me kike nufi shiɗin ba Uwa da Ubane suka haifeshi ba shima ɗana ne”. Sheƙeƙe Hajiya Karima ke Kallonsa kafin cike da Isgilanci ta kallesa kana tace. “Yaushe ka haifesa bamu da labari?,yaushe ka auri uwarsa har ka haifesa bamu sani ba?”. Cikin tsananin fushi Abba yace. “Kifita anan ki fita Karima bana son ganinki tun da ke kince baki da ɗa'a baki iya Mu'amala da mutane arayuwarki ta duniya ba, bana son haka, Bana son haka kar ki sake yin haka na yi miki kashedi na ƙarshe wannan shine last warning Hajiya Karima!, Kada ki sake yimin haka. Domin kuwa koda Mahaukaci Jameel ya ɗauko ya kawo wannan gidan wallahi yafi min ke daraja, saboda nasan koda mahaukacine Jameel zai nuna masa cewa ni mahaifinsa ne kuma na tabbata zai mutunta ni”. Cikin fushi ya sauƙe ajiyar zuciya tare da furzar da Iska kana ya cigaba da cewa. “Na tabbata ko Mahaukaci Jameel ya kawo gidan nan zai mutuntani, kuma zai ɗauke ni da daraja fiye da yanda ke ki ɗaukeni ban isa da keba, misali ga yadda idan na baki umarni kike fatali dashi, ba zakiyi amfani dashi ba. Dan haka ko kin san Jameel ya fimin komai. Jameel da kike gani shine Komai nawa a Duniya akan farin cikin Jameel ina iya yin komai dan haka tun wurima ki kiyayeni! Kifita idona in rufe Hajiya Karima!!. Ki kiyayeni kada inci miki mutunci!!!”. Ya ida mgnar tare da buga jikin kujerar dining ɗin kana yaci gaba da cewa. “Na tabbata kare idan Jameel zai kawo gidan nan sai yamin biyayya fiye da yanda ke kike min biyayya. Kare dai nasan idan Jameel zai kawo min gidan nan bazai tsaya yamin irin haushin da kike min ba!”. Sai kuma ya watsa mata Kallon mai cike da fushi kana yace. “Kare idan Jameel zai kawo gidan nan kare mai ɗa'a da biyayya zai kawo min ba karen da zai kunya ta min baƙi na ba amma ke kullum baki da hankali. idan Jameel ɗan kine da kika haifa acikin ki zaki yi masa haka ne?”. Kasa cewa komai Hajiya Karima tayi sai huci da take tamkar zakanya. M Jameel kuwa ƙasa yayi da kansa cike da jin daɗi karo na farko kenan da mahaifinsa ya burgesa a kanta daya buɗewa Hajiya Karima wuta akan abinda ta keyiwa Moddibo domin kullum idan ta wulaƙanta Moddibo sai sunbar gidan kafin yake mata faɗa akan ta daina, amma yau yaji daɗin faɗan da Abba yayi mata agaban Idon Moddibo saboda Moddibo zaiji daɗi sannan zai san cewa yana da daraja da kuma kima awajensu. Moddibo kuwa kansa ya sunkuyar ƙasa da cike kunya sam baiji daɗin ɓatawan mata da Miji adalilinsa ba, yayi dana sanin zuwa gidan, yasan cewa duk lokacin da yazo gidan sai yayi sanadin da za'a samu hatsaniya, sannan ya riga daya sani tun yana yaro matar nan bata sonshi bata ƙaunar ganinsa da Jameel sai dai ya fahimci ba wai shi ta tsana ba tana fakewa da guzma ne ta harbi karsana. Cikin sanyi murya ya ɗago kansa tare da furzar da iska mai zafi kana yace. “Abba kayi haƙuri dan Allah dan darajar Annabi”. Juyawa Abba yayi ya kallesa kana ya ɗaga masa hannu da faɗin. “Yi shiru ba maganar ka Aliyu barni da ita haka take yimin, ba kai kaɗai ba, duk baƙon da Jameel zai kawo gidan nan sai taci masa zarafi, duk mutumin da zata gansa da Jameel saita nuna min ba mutumin kirki bane!”. Sai kuma ya juyo Afusace tare da kallonta har zuwa lokacin tana tsaye cike da ɓacin rai ya tsira mata idanu kana yace. “Mai Jameel ya tsare miki?, Jameel tun tasowar yana ƙarami biyayya yake miki bai taba Musa Miki ba duk da kinzo kin samu yana da shekara goma sha huɗu na tabbata baki yiwa Jameel wahala ba amma yana karramaki sannan yana mutuntaki kamar yanda yake mutunta mahaifiyarsa”. Zazzafan iska ya furzar kana still muryarsa cike da ɓacin rai yace. “Amma ke kullum baki da buri daya wuce kici masa zarafi, Idan kin zauna ki riƙa faɗa mun magana kinyi zaton cewa bana son Jameel ne?. Shin inada wani ɗa aduniya daya wuce Jameel ne?”. Cikin tsananin fushi da ɓacin rai Hajiya Karima ta nuna kanta kana tace. “Ni ka ciwa zarafi akan yaro ɗan maƙota dan yana abokin ɗan ka, sannan dan na faɗa maka gaskiya, kai baka ga yadda yake liƙewa ɗan nakaba duk ya hana sa tattalin arziki sannan ya hanasa ya tara abin kansa”. Cikin wata fusatacciyar tsawa daya amsa ilahirin falon yace. “Ki fice min anan Karima bana son ganinki”. Afusace ta juya kamar zata tashi sama tana wani irin huci tare da jin tsanar Moddibo da M Jameel fiye da komai arayuwarta!. Anutse Abba ya juya ya kalli Moddibo kana cikin sanyi murya yace. “Dan Allah Aliyu kayi haƙuri kada ka damu da abinda tayi maka, sannan bance ka ɗauki wannan amatsayin wani mataki da zai hana ka zuwa gidan nan ba, aduk sanda kaga dama zaka zo”. Murmushi yayi kana yace. “Babu komai Abba ai ita mahaifiya ce agurin mu dan tayi mana haka ba zai zama wani aibu ba”. Jinjina kai Abba yayi tare da cewa Ubangiji Allah ya al'barkaci rayuwarku”. Atare suka amsa da. “Ameen”. Juyawa M Jameel yayi tare da kallon Moddibo Cikin sanyin murya mai cike da so da shaƙuwa ya numfasa kana yace. “Dan Allah A.J kayi haƙuri”. Murmushi Moddibo yayi kana yace. “Laa babu Komai J. Yanzu dai tashi muje mu bata haƙuri”. Da sauri Abba ya kalli Moddibo kana yace. “Baza ku bata haƙuri ba ku zauna kuci abinci”. Kai suka gyaɗa sannan suka zauna baki ɗayansu, basu wani ci abincin kirki ba, domin ko kowa da irin damuwar dake ransa, bayan sun kammala suka miƙe tare da yiwa Abba Sallama haƙuri Abba ya sake bawa Moddibo. Murmushi Moddibo yayi kansa aƙasa yace. “Ayyah Abba Allah babu komai”. Sannan suka juya har sun kai ƙofa Abba ya ɗan ɗaga sautin muryansa tare da cewa. “Yau kam ba zamu kwana anan bane?”. Girgiza kai Moddibo yayi kana yace. “A'a Abba idan mun kwana anan Innayi ita kaɗai zamu bari acan”. Jinjina kai Abba yayi kana yace. “Eh kam ya kamata gida babu namiji ba gida bane kuje”. Godiya suka masa kana suka fice. Suna cikin mota aka kira Isha'i kai tsaye masallacin da suke limancin suka nufa kamar ko yaushe Moddibo ne yaja Sallar bayan sun idar sukayi Asham kana suka wuce gida. Suna shiga gida kai tsaye sashen Innayi suka nufa zaune suka sameta riƙe da carbi ahannun Asma'u kuma tana riƙe da Alkur'ani mai girma tana karatu. Batare da sun ƙarasa shiga ba Moddibo yace. “Innayi Barka da shan ruwa”. Anutse ta kallesa kana tace. “Yawwa yau ina kuka tsaya ne baku dawo da wuri ba, nace Asma'u ta kira min ku inji kuma ashe wayar ba kati”. Murmushi M Jameel Yayi kana yace. “Ayya Innayi Abba ne ya kiramu wai muje mu sha ruwa acan shiyasa kika jimu shiru”. Kai ta jinjina tare da kallon Moddibo tace. “Fatan duk suna lafiya?”. Kai Moddibo ya gyaɗa mata kana ya sake labulen tare da faɗin. “Innayi akawo mana abinci”. Ya ida mgnar tare da zama akan shimfiɗar dake barandar Asma'u Innayi ta ƙalla kana tace. “Ɗauki abincin ki kai musu”. Kai Asma'u ta gyaɗa sannan ta ɗauki lemun tsani ta yanka ta matsa kaɗan akai kana tayi slinzing ɗin ƙwoyi kana ta zuba musu wadataccen man gyaɗa da kuma dakekken yajin barkono sai Cucumber da Cabbage ta Kai musu. Sosai suka Moddibo da M Jameel suka ci ɗan waken tare da 5alive, bayan sun kammala kai tsaye ɗakinsu suka wuce tare da watsa ruwa, kana suka sake shiryawa tare da feshe jikinsu da turaraku masu daɗin ƙamshi. Cikin nutsuwa suka fito aharabar gidan suka samu Innayi da Asma'u sun fito buɗe bayan motor sukayi suka shiga sannan Moddibo ya shiga mazaunin Driver yayin da M Jameel yashiga gefen mai zaman banza, kai tsaye masallacin suka nufa har suka isa ƙira'a na tashi amotar suna parking Innayi da Asma'u suka shiga sashen mata suka ma suka ƙara sa sashen su. Yau ma kamar kullum gaba ɗaya cikin masallacin da harabar sa cike yake da ɗumbin jama'a cikin tsantsar nutsuwar daya zame musu jiki suka nufi wajen zamansu cikin sanyi mai cike da kamala da kuma kamun kai Moddibo ya ajiye System ɗin sa kana ya zauna tare da ɗan jingina bayansa da jikin kujeran ya lumshe Idanunsa tare da motsa laɓɓansa alamar tasbihi Shikuwa M Jameel zaman microphone da aka dasa masa ya gyara tare da buɗe System ɗin sa Lokaci ɗaya cikin masallacin ya gauraye da ƙamshin sanyayyan turaren su yayin da hasken Fararen glob ɗin ya haskaka hasken farin fuskarsu na fitar da sheƙin annuri yayin da baƙin sajensu ya kwanta luf-luf komai nasu kusan ɗaya yake tamkar tagwaye. Cikin nutsuwa M Jameel ya lumshe Idanunsa tare da gyara zaman Microphone kana Yayi gyaran murya cikin Sanyayyar muryarsa mai cike da kamala yayi gyaran murya kana yace. _“Innalhamdulillah Nahmaduhu Wanastainuhu wanastaghfiru wa'nazubillahi billahi min shuriri anfusna wamin sayyi ati a'amalina manyah dillahu fala hadiyala waman yudil fala mudillalah Wa'ash hadu Allah ilahalillahu wahdahu lasharika Wa'ash hadu anna Muhammadu Abduhu warasulu Ya Ayyuhal lazina amanut taƙullaha haƙƙu tuƙatihi wala tamu tunna illah wa'antum muslimun Ya ayyuhan nasu taƙu rabbakummalazi halaƙakum min nafsi wahida wahalaƙa minha zaujuha wabassa min huma rijalan kasiran wa Nisa'a wattaƙullahal lazi tasa aluna bihi wal arhama innalaha kana bikum raƙiba, Amma ba'ad faya Ikhwatul musulmi Assalamu alaikum warahmatullah wabarkatuhu”_. A tare jama'ar dake cikin masallacin suka amsa da. “Wa'alaikum Salam warahmatullah wabarkatuhu”. A hankali M Jameel ya fesar da sassayan numfashi tare da lumshe idanunsa kana a hankali yace. “A yau muna sha huɗu ga watan Ramadan a cigaba da tafsirin Alkur'ani mai girma da muke acikin masallacin mai Martaba sarki Bashiru acikin Suratu An-Nisa'i ayau zamu tashi akan aya ta Cassa'in da huɗu wala Allah kuma bazai wuce da biyar zamu tsaya ba, sai kuma shekara mai zuwa idan Allah ya bamu aron rai da lfyar”. Sai kuma ya sauƙe numfashi kana ya cigaba da cewa. “Tun daga kan aya na cassa'in da biyu muka shiga babi akan kashe ran mumini, da kuma hakkin ran Muminai, ayau Insha Allah zamu cigaba, amman kafin nan zamuyi duba i zuwa kan dukkan ayoyin Alkur'ani dake mgna kan ran muminai”. A hankali ya buɗe kwayar idanunsa, sabida jin yadda masallacin ya cika da kabbara. Gyara system ɗinshi yayi kana yace. “Insha Allah ayau Aramma zai zaƙulo mana Ayoyin da Ubangiji yayi magana akan hakkin kashe ran mumini, domin tunatar wa da kuma jan hankali da kuma fito da darajar ran ɗan Adam Dan kiyaye lalacewar zamani da kuma tunatar da hakkin ran musulmi amatsayin ba komai ba”. Cikin yanayin kamala ya juya tare da maida kallonsa kan Modibbo da idanunsa ke lumshe ajiyar zuciya sauƙe kana yace. “Aramma bamu ayoyin da Ubangiji yayi magana akan kashe ran mumini”. Anutse Moddibo ya gyara zamansa tare da ɗan ture system ɗin sa gefe kana yayi gyaran murya cikin sanyayyar sautin muryarsa ya fara kamar haka. Surah Al-ma'idah Aya 32 مِنْ أَجْلِ ذَٰلِكَ كَتَبْنَا عَلَىٰ بَنِي إِسْرَائِيلَ أَنَّهُ مَن قَتَلَ نَفْسًا بِغَيْرِ نَفْسٍ أَوْ فَسَادٍ فِي الْأَرْضِ فَكَأَنَّمَا قَتَلَ النَّاسَ جَمِيعًا Ya ƙare jan karshen ayar da fesar numfashinsa da ya riƙe domin fidda cikekken haƙin ko wanne harafi, Yayin da Al'ummar Annabi dake cike a masallacin kuwa, sukayi sit suna masu samun cikekkiyar nitsuwa ta mu'ijizan jin karatun Alqur'ani mai girma kenan. M Jameel kuwa cike da raunin murya ya fara fassara ayar Allah madaukakin sarki nacewa-: “Sakamakon haka ne muka wajabta akan 'ya'yan Isara'ila cewa, duk wanda ya kashe wata Rai ba tare da ita Rai ɗin ta kashe wata ba, ko kuma yayi ɓarna a kan ƙasa (ta'addanci, Fashi da makami etc) toh kamar ya kashe mutane ne gaba ɗaya na Duniya kuma ubangiji zai hukunta shi dai-dai da laifinsa”. Shiru masallacin yayi baki ɗaya, kowa jiki nai a mace, yayinda manyan dottaɓai dake ciki kuwa, suka zuba M Jameel da Modibbo ido suna nazartan yadda akayi akalar tasirin ya sauya daga kan Suratu An-Nisa'i ya koma kan duk ayar da ke mgn kan kisan kai. Shi kuwa M Jameel juyowa yayi ya kalli Modibbo tare cewa. Aramma koma cikin suratul Al-ma'idah akwai ayar da Allah ke mgn kan rayuka”. Cike da ƙwarewa da cikekkiyar hadda mai ɗauke da kaifin basira, Modibbo ya lumshe idanunsa da yakeji suna cika da rauni cike da zaƙin murya ƙira'a mai sa nitsuwa ya kawo ayar Surah Al-ma'idah Aya 33 إِنَّمَا جَزَاءُ الَّذِينَ يُحَارِبُونَ اللَّهَ وَرَسُولَهُ وَيَسْعَوْنَ فِي الْأَرْضِ فَسَادًا أَن يُقَتَّلُوا أَوْ يُصَلَّبُوا أَوْ تُقَطَّعَ أَيْدِيهِمْ وَأَرْجُلُهُم مِّنْ خِلَافٍ أَوْ يُنفَوْا مِنَ الْأَرْضِ. Cike da nitsuwa ya dire ƙarshen ayar, M Jameel kuwa gyara zamansa yayi tare da fara fashin baƙin. “Allah madaukakin sarki nacewa-: Lallai sakamakon waɗanda suke yaƙar Allah da Manzo nai, kuma suke yaɗa ɓarna a doron ƙasa (ta'addanci, Fashi, ƙwamushe Garkuwa Da mutane etc), shine a kashe su, ko a giciye su”. Sai kuma ya fesar da sassayan numfashi tare da lumshe idanunsa wanda tuni suke sheƙin ruwan hawaye, murya cike da rauni yaci gaba da cewa. “Ko a yanke Hannayen su da Ƙafafuwan su a saɓani (hannun hagu da ƙafar dama, ko kuma Hannun dama da ƙafar Hagu), ko kuma a kore su daga Garin.”. Zuwa yanzu shar-shar hawayensa ke kwaranya yayinda tuni muryarsa ke rawa, haka yasa da yawa mutanen suke zubda hawaye. Haka dai Modibbo ya rinƙa zaƙulo dukkan ayoyin Alkur'ani dake mgna kan ran mumini, M Jameel na fassarawa, yayinda gaba ɗaya zuƙata jama'ar masallacin ya cika da rauni. Kasan cewar gobe ne, Modibbo da M Jameel ɗin zasu wuce ƙasa mai tsarki, damin yin Umrah Ramadan, yasa dole a ranar aka rufe tafsir ɗin. Bayan jero Addu'o'in wa al'ummar musulmi dama kasa baki ɗaya. Washe gari ranar 15 ga watan Ramadan misalin ƙarfe tara na dara dai jirgi su Modibbo ya tashi daga cikin Taraba zuwa ƙasa mai tsarki...! Daga yauwa ɗin nan Laraba mun gama free page, in kina son ci gaban littafin SAKAYYAH to ki biya ki karanta cikin aminci. Littafin SAKAYYAH 1k ne kacal 0661110170 GTBank AISHA ALIYU GARKUWA, sai ki turo min shaidar biyanki ta WHATSAPP 09097853276. Ki biya ki karanta ba haƙƙin kowa a kanki. By *GARKUWAR MARUBUTA* [19/07, 8:57 PM] Halimatu A/rahman Sadeeya: 📝✨💫⏰🤴🏻👹❤️❤️❤️🍇 *SAKAYYAH* _Page 17_ *LAST FREE PAGE* _NA_ *AYSHA ALIYU GARKUWA* 🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 *DAGA WANNAN PAGE ƊIN FREE PAGES SUN ƘARE, IN MA KIN SAKE GANIN LITTAFIN SAKAYYAH A WAJE TO. NA SATANE NA ALLAH YA ISA ne, littafin SAKAYYAH 1k ne kacal yar ki biya ki karanta cikin Aminci da salama babu haƙƙin kowa kanki 0661110170 GTBank AISHA ALIYU GARKUWA sai ki turo min shaidar biyanki ta WHATSAPP 09097853276 kiyiwa da Annabi in dai kin san kin sayane don ki fitarmin da littafin na kiyi min mgn in mayar miki da kuɗinki. In kuma kin san zaki sayane dan ki fidda min littafina, wasu Groups ɗin, kiyiwa Allah da Manzonsa ki bar kuɗinki na yafe cinikin bana buƙatar sa* Alhamdulillah su Moddibo sun sauƙa lfy a ƙasa Mai Tsarki cikin ikon Allah Mabuwayi gagara Misali sunyi Umarah sun samu goma shabiyar na watan acan cike da ɗumbin farin ciki. Yau yakasance ranace ta Sallah angama azumi lfya. Al'ummar Musulmai na duniya sun cika da farin ciki kowa kagani fuskarsa ɗauke da yalwataccen farin ciki, kana kowa yayi shiga ta haiba da kamala. Alhamdulillah bayan an saƙƙo daga sallar idi ko wani gida kashiga zaka samesu cikin farin ciki da shiga ta kamala kana da Lafiyayyan abinci. Kamar yanda ko ina na faɗin duniya ya cika da farin cikin wannan ranan haka yakasance Agidan Lamiɗo. Acan falon Mommy kuwa hallare suka gaba ɗayan su Khausar ce tsaye riƙe da waya ahanununta cikin shiga ta alfarma da kamala wani rantsatstsen less ne Blue da ratsin fari ne ajikinta ɗinkin riga da skirt yayin da skirt ɗin ya fitar mata da shape din ƙugunta rigan kuwa tayi ɗass ajikinta ma dai-dai-tan dukiyar fulaninta sun cika fam yayin da tayi ɗaurin ƴar Minister ta zubo yalwataccen sumar kanta zuwa baya daga gaban goshin kuwa ya kwanta luf-luf wuyanta maƙale da sarƙan Gwal da ɗan kunnensa kana fuskarta ɗauke da simple make up daya sake ƙawata kyawun fuskarta. Yayin da Raudat ma ke sanye cikin irin shigar dake jikin Khausar sai dai nata ɗinkin dogon riga ne. Haiydar kuwa sanye yake cikin wata Bugaggiyar shadda Sky blue anyi masa ɗinkin samarin zamani rigar ta tsaya iya gwiwarsa, kansa sanye da hula yalwataccen sumar irin na fulanin Usul yana kwance lib aƙeyarsa haka ma Ramadan sanye yake cikin irin shigar Haiydar Yayin da Mommy ke sanye cikin Atanfa mai Golden mai masifar kyau anyi mata ɗinkin riga da zani fuskarta ɗauke da simple make da Khausar tayi mata. Baki ɗaya falon wani sanyayyan ƙamshi yake fitarwa wanda ya haɗu da ƙamshin jikinsu. Cike da tsantsar farin ciki Khausar dake ɗaukar su hoto ta juya ta kalli Mommy kana tace . “Kuce Chesss”. Dariya suka fashe dashi kana suka ce. “Cheeessss”, Akuma dai-dai lokacin ta ɗauki hoton. Sosai hoton yayi kyau kallo ɗaya zaka musu ka tabbatar da cewa suna cikin tsantsar farin ciki da annushawa tare da nutsuwa. Suna cikin hoton Hajiya Bunayya tashigo cikin shiga ta alfarma da kamala sosai tayi kyau. Zama tayi bayan tayi Sallama Idanun ta akan Mommy tace. “Barka da Sallah ƙanwata fatan anyi Sallah lafiya?”. Murmushi Mommy tayi kana ta zauna kusa da ita tare da cewa. “Ayyah Yaya ina shirin zuwa wajenki ma”. Murmushi Hajiya Bunayya tayi kana tace. “Ayyah babu komai nima cewa nayi bari na rigaki zuwa in samu ladan gaisuwar. Fatan munyi Sallah lafiya?”. Jinjina Kai Mommy tayi kana tace. “Lafiya Lau Alhamdulillah Yaya Ubangiji Allah ya amshi ibadun da ayyukanmu na Al'khairai Allah ya nuna mana na baɗin baɗaɗa da rai da lafiya”. Kai Hajiya Bunayya ta gyaɗa kana tace. “Ameen ya Allah Ƙanwata”. Khausar kuwa kallo ɗaya tayi mata ta kawar da kai gefe. Hajiya Bunayya kuwa kallonta ta mayar kan Khausar dake ɗaukar Haiydar, Ramadan, da Raudat hoto, cike da makirci tayi wani murmushi kana tace. “Khausar Barka da Sallah”. Anutse Khausar ta juya ta kalleta babu walwala afuskarta muryarta ta saisaita kana tace. “Yawwa Barka dai Ummah”. Hajiya Bunayya ta mayar da kallonta kan Haiydar dake tsaye gefenta hannunsa ta kama tare da damƙa masa key da murmushi afuskarta tace. “Ga Barka da Sallah ka Babana”. Zare ido Haiydar yayi tare da buɗe hannunsa ya kalli sabon key ɗin mashin dake cikin tafin hannunsa, cike da tsananim farin ciki mara misaltuwa ya faɗa jikin Hajiya Bunayya tare da rungumeta cike happy ya saƙi ƙara kana yace. “Wayyo Ummah na Nagode. Allah ya saka da al'khairi. Allah yaƙara miki nisan kwana mai amfani. Allah yarabaki da sharrin Mutum da Aljan, gaskiya nayi farin ciki kinyi surprise ɗina da kince sai bayan Sallah da kwana biyu. Cike da farin ciki tayi murmushin gefen baki kana tace. “Ameen,Ameen Babana, Eyyyy dama sunce sai bayan Sallah da kwana biyu sai kuma suka kawo jiya da daddare”. Khausar kuwa cike da takaicin halayyar matar ta riƙa watsa mata harara wani irin haushin ta takeji, aƙasan ranta kam cewa take shegiya muguwa aniyar ki ta biki da izinin Allah babu abinda zai samesa. Mommy kuwa kallon Khausar dake bin Hajiya Bunayya da harara tayi kai ta girgiza tare da cewa. “Khausar jeki ɗauko mana abinci a kichen ki kawo kin tsaya kin tsare mutane da ido baza ki iya taya ɗan uwanki samun abin farin cikin da yayi ba”. Zumɓura baki Khausar tayi tare da miƙewa batare da tace Komai ba tashiga kichen. Haiydar kam Kallon Mommy Yayi kana yace. “Mommy Ummah ku tashi nayi muku hoto”. Miƙewa sukayi da murmushi afuskarsu Haiydar yashiga ɗaukar su. Khausar kuwa fitowa tayi hannunta riƙe da Warmers dake ɗauke da soyayyun kaji ta ajiye a dining kana ta koma ta sake ɗauko wasu Warmers ta ajiye. Dai-dai lokacin da Mommy ke cewa. “Yaya mun gode sosai Allah ya saka da alkhairi Agaskiya nayi farin ciki”. Fuskar Khausar ta ɓata kana tace. “Haba Mommy irin wannan godiyar sai kace wacce aka biyawa Kujeran Hajji”. Kallonta Mommy tayi kana tace. “Ai kujeran hajjin ne Khausar, mutumin daya so ɗan ka arayuwa har yayi masa alkhairi ai babu kamarsa ”. Kai Khausar ta girgiza kawai aranta tace Mommy har yanzu baki san wacece wannan makirar matarba, shiyasa kike yabonta wannan matar da kike gani tafi kwalba sharri afili kuwa cewa tayi. “Hmmmm Allah ya kyauta”. Murmushin da be wuce saman laɓɓaba Hajiya Bunayya tayi kana ta miƙe tare da cewa. “Nikam zan wuce”. Miƙewa Mommy tayi tare da cewa toh mungode Yaya Allah yaƙara girma da ɗaukaka”. Ita kuwa Hajiya Bunayya ficewa tayi Yayin da Haiydar yabi bayanta zuwa sashen Lamiɗo. yana shiga yace. “Abba gashi Ummah ta siya min Mashin zan hau?”. Kai Lamiɗo ya gyaɗa kana yace. “Babu damuwa tun da kana son hakan, amma kafin nan sai an sake koya maka mashin ɗin na tsawon wata biyu kafin ka fara hawa kai ɗaya kaga ai ka sake koya”. Jinjina kai Haiydar yayi kana yace. “Toh shikenan Abba babu Matsala ”. Bayan sallah da kwana biyu jirginsu Moddibo ya sauƙa a Nigeria cike da farin ciki Moddibo, Innayi da M Jameel Ummi suka dawo gida yayin da Hajja Nana ma ta sauƙa ta Ɓadamaye cike da farin ciki da kuma murna. ********** Ahaka rayuwa ta cigaba da tafiya komai yana tafiya dai-dai cikin ikon Allah Akwana atashi asaran mai rai, sekonni na juyawa izuwa Mintuna, Mintuna na tafiya izuwa awanni. Yayin da awanni ke juyawa izuwa kwanaki, kwanaki na tafiya izuwa Makonni. Yayin da Mokonni ke juyawa izuwa Watanni. A hankali kuma watanni ke tafiya Izuwa shakara ko shekaru... Alhamdulillah su Khausar sunyi nisa kiwo aski yazo gaban goshi, yanzu suna shirye shiryen zana jarabawar Ƙarshe na kammala secondary School WEAC and NECO baki ɗaya kansu ya ɗauki zafi basu da wani lokaci saina karatu sosai suka maida hankalin su suna karatu tuƙuru domin fitowa da kyakkyawan sakamako Inda yanzu ya rage saura Exam biyar ya rage su kammala Neco. Khausar ce tsaye gaban Dressing mirror jikinta ɗaure da towel da tsawon sa ya kai gwiwarta, Zuwa yanzu ko ina na jikinta ya cika fam, dukkan ƙirar girma maƙerin budurci ya ƙenƙesa matashi, musamman Dukiyar fulaninta da kuma hips dinta da suka cika ƙugunta, yalwataccen sumar kanta irin na Fulanin Usul ya sake tsawo da sansti. Manyan Idanunta sun sake girma tare da lumshewa siririn dogon hancinta ya sake tsawo yayin da madaidaicin bakinta ya sake tattarewa izuwa pich collor, yana yin ƙiranta kamar kolbar Coca cola Yayin da Tsananin kamanninta da Kajol ya sake bayyana ayanzu tana da shekara goma sha tara a duniya. Cikin sauri ta shafa Lotion ɗin ta tare da shafa powder sama-sama sai kuma ta shafa kwalli amanyan Idanunta lipstick kaɗan ta shafa asaman laɓɓannta cikin sauri sauri ta sanya Uniform ɗin ta daya sha guga tulin sumar kanta tayi acuci dashi kana ta feshe jikinta da turarukanta masu masifar daɗin ƙamshi da sanya nutsuwa. Cikin Sassarfa ta fito falo harara Mommy ta maka mata kana tace. “Ke dai Khausar ba zaki canza ba kin girma amma kullum shiririta kike ƙarawa tun yaushe Ake jiranki, ga Amina ma can tanata jira amma sai ɓata musu lokaci kike”. Langwaɓar da kai Khausar tayi tare da riƙe kunnenta kana tace. “Sorry Mommy”. Fuska ta tsuke tare da ce wa. “Kin dai san Amina in ta gaji da jiran ki”. Cikin ɗan sauƙe numfashi tace. “Uhumm ai yaseen in ta gaya min mgn ramawa zanyi in banda asarama tun tuni yaci ace ta gama, amman kullum taba cikin dakon aji har wai sai yanzu zamu gama tare”. Mommy na juya zata fita tace. “A'a ni bana son fitina”. Ta ida mgnar tana fita, Haka yasa ta biyo bayan Mommy da ɗan sauri yayin da ko wanni gaɓa na jikinta ke motsa wa baki ɗaya alamun Budurci sun bayyana ajikinta ta ko wanni fanni ta zama cikakkiyar budurwa ƴar gayu First class. Bayan motar ta buɗe ta shiga bayan ta ƙarasa wajen gani tayi duk Amina ta wani babbaje. Kamar ba zata ce komai ba sai kuma tace. “Ɗan matsamin in zauna”. Kallon banza Amina ta watsa mata cikin ya mutse Fuska ta kalli Khausar kana tace. “Keɗin har nawa kike da wannan wajen ba zai ishe ki ba?”. Cikin juya ido tace. “Kinsa cikakkiyar sura ta ƙasaitattun mata Allah ya min dole wurin bazai isheni ba tunda ba irin baki bane”. Cike da fusata Amina tace. “Eh lallai yarinyar nan wuyanki ya kai yanka, amman dadin ta dai bada ɗuwawunki nake zamaba kuma bada ƙugunki nake ɗaura zabi ba”. Taɓeki tayi tare da juyawa ta kalleta. Har kamar zata yi magana sai kuma ta fasa ganin yanda lokaci ke tafiya sannan ya Exam na Geography zasuyi tasan muddin aka fara Moddibo na iya hukuntata baya ga haka ga kuma alamun yau akwai hadari a garin wanda yau kimanin kwana tara kenan ba'ayin musu ruwan saman ba. Gefen Haiydar ne ya matsa mata ta shiga kana Driver yaja suka tafi. Suna Isa Khausar tayi saurin ficewa tare da nufar Hall da zasu zana Exam ta nufi Hall ɗin yayin da Iska mai sanyi ya soma kaɗawa gari ya fara duhu suna cikin rubuta Exam ɗin hadari ya fara haɗa gangami sosai a hankali gari ya fara duhu. Basu wani ja lokaci ba suka kammala rubuta Exam ɗin atare Khausar da Asma'u suka fito. Asma'u ma ta zama cikakkiyar budurwa komai na Budurci ya bayyana ajikinta. Juyowa Khausar tayi ta kalleta ƙirjinta rungume da Questions da suka gama rubutawa, murmushi ta ɗan yi kana tace. “Asmeey ki gaida min Ummi dan Allah, wallahi nayi missing ɗinta, rabo na da ita fa ya kai wata biyu”. Hararanta Asma'u liƙa mata kana tace. “Ai baki da kirkine sannan babu saƙon ki da zan fada mata in da gaskene kizo”. Ta ƙare mgnar tana mai ɗaga kanta ta kalli sama, ganin yadda gaba ɗaya garin ya rufa yayi duhu. Da sauri Khausar ma ta fara juye-juye tana cewa. “Yah Salam wannan hadari haka, ina Haiydar suzo mu tafi, kar ruwa nan ya rutsamu a nan.” Murmushi Asma'u tayi tare da cewa. “Allah yasa ya rutsa kin dai muga ta tsoro”. Ta ida mgnar tare da yin murmushin mugunta dan tasan yadda Khausar ke masifar tsoron walƙiya da tsawa. “Ba Amin ba”. Khausar ta faɗa tare da tura baki. Ita kuwa Asma'u dariya tayi tare da jan hannun Bashir sukayi gaba saboda yanda hadarin ke sake gangami ko ina yayi ɗib. Murmushi Khausar tayi kana tace. “Bashir dan Allah kagaida Ummi, dan naga yau mutuniyar Black Stomach take ji dashi”. Asma'u na ƙoƙarin shiga mota tayi murmushi kana tace. “Oho dai ance zuwa da kai ai yafi saƙo”. Khausar kuwa murmushi tayi tare da bin bayansu ganin Haiydar yayi gaba. Da ɗa sassarfa ta tashiga bayan motar ta zauna kusa da Haiydar tana ɗan kallon harabar makarantar da duk aka watse sai mutane ɗaɗɗaya har malamai da alamun sun tattafi da sauri ta juya ta kalli Haiydar kana tace. “Ina Amina kuma?”. hannu ya buɗe mata alamar bai sani ba, bata sake cewa komai ba, ta lumshe idanunta tare da jingina bayanta da jikin Kujeran sassayan iskan hadarin dake bugawa na ratsata. Acan harabar makarantar kuwa Amina ce da Samira Sani ke tafiya. Cikin taɓe baki Samira ta kalli Amina kana tace. “Ni wallahi tunda nake ban taɓa kallon mutum Irin Moddibo ba ace mutum kamar dutse sam baya fahimtar komai”. Murmushi Amina tayi kana tace. “Hmmm ke dai Samira bari M Jameel ɗin ma meyene, duk tsawon lokacin da muka ɗauka muna aiki da maganin fa yanda yake wani shan min Ƙamshi”. Harara Samira ta watsa mata cike da takaici tace. “Amma Wallahi Amina baki da godiyar Allah ki dubi yanda mutumin nan ya fara sake miki, yana amsa gaisuwar ki da fara'a, yana kula ki da ace nice nasamu wannan damar, awajen Moddibo ai dana godewa Allah”. Jinjina kai Amina tayi kana tace. “Haka ne kuma amma gaskiya har yanzu sai mun sake sabon shiri akansu domin har yanzu Malam Jameel yafi ji da wannan shegiyar yarinyar akaina”. Da wannan hira suka isa jikin motar wani matsiyacin kallo Amina ta watsawa Khausar dake bayan mota Idanunta alumshe cike da gadara da kuma Izzah ta ya mutse fuska kana tace. “Iyeee ƙarfin hali yau naji Agola da ƙarfin hali, motar na gidan Ubankine da zaki shiga baya kiyi kane-kane aciki, to ni kuma a ina zan zauna ji yanda kika tara ƙannenki kuka lafe abaya ku gaku ramukan kura ko daga ke sai ƙannen ki, wai ma tukunna ni akanki zan zauna ne!? Da kika wani baza masaka-masakan duwaiwaka”. Ahankali Khausar ta buɗe Idanunta dake lumshe ta zuba mata su tana kallonta cike da mmki, amma ba tace komai ba sai gyara zamanta da tayi tare da buɗa mata inda zata zauna. Ya mutse fuska Amina tayi cike da jaraba da kuma gadara ta dubi inda Khausar ta matsa mata kana tace. “Wannan wani irin iskanci ne da raini ne ko kuma ni sa'ar kice ke badan kinyi sa'ar Babanki ya mutu ya bar uwarki tayi zawarci babana ya kwasa ba ai koda hanyar da nabi baki isa ki biba. Agola kawai mara galihu ƴar matsiyata”. Cike da ɓacin rai Khausar ta ɗago kanta babu walwala afuskarta ta kalli Amina tare da cewa. “Wai Meyesa kike son zagina ne? Baga shi na gyara niki ba wannan ɗan ɗuwawun da kamar an ɗaurawa kare zani me zai hana filin isarki, baki shigo kin zauna kinga wurin bai ishi tsamurarrun mauzanki da suke kamar an matse lemon tsamiba kawai saboda kin saba da Akuyanci da kuma karnukan ci sai kin tsaya anta masifa dake da raba hali, saboda ke Jaka ce baki san darajar mutane ba, zaki tsaya kina ta goranta min akan wani Akwalar mota! To ki sani ni dai bazan zagi iyayenku ba musamman mahaifinki da yake mumini uwarki kuwa zaginta ma asarane don ko zagi akan mai tsarki yake fatan a aikeshi”. Harara Amina ta watsa mata kana Afusace tace. “Eh koda Akwalar ce aiba Ubanki bane ya saya idan kuma Ubankine ya saya sai inji? koda yake nasan har matsiyacin Ubannaki ya mutu bai taɓa mallakar irin wannan na kansa ba!”. Cike da matsanancin ɓacin rai Khausar ke kallonta idan akwai abinda tafi tsana aduniya kana yake saurin fusata ta shine zagin mahaifinta. Azuciye ta sauƙa daga motar yayinda Haiydar da su Ramadan ma suka sauƙo, cikin nuna Amina da yatsa tare da ƙanƙantar da idanunta kana tace. “Kada ki sake zagin Ubana domin Ubana yafi ki daraja koda Agaban Ubangiji”. A yatsine Amina ta watsa mata mugun kallo kana tace. “An zage sa ƴar iskan yarinya mai hana ruwa gudu ƴar matsiyata”. Cikin wani irin fushi Khausar ta ɗaga hannunta tare da kife Amina da wani irin azabebben mari hagu da dama cikin nunuta da yatsa tace. “Ki sake zagar min Uba kiga abinda zan gwada miki”. Dafe kuncin Amina tayi cike da Mamaki take kallon Khausar kana tace. “Ni kika mara Khausar?”. Harara Khausar ta watsa mata da manyan Idanunta kana tace. “An mare ki”. Ahankali Habu Driver ya leƙo kansa tare da faɗin. “Khausar kiyi haƙuri". Sai kuma ya kalli Amina dake huci kana yace. “Amina kema sam baki kyauta ba taya zaki zagi Ubanta ai duk Abinda zakuyi tsakaninku ne”. Wani shegen kallo ta watsa masa Afusace tace. “Habu ka rufe min baki ka fita Idona na zagi Uban nata idan taji haushi tabar mana gidan mu ta tafi gidan Ubanta ƴar matsiyata ƴar jarababbu Angola ta bar nan garin ta koma can dajin nasu mana”. Ta ida maganar tare da shiga motar taja murfin ta rufe da ƙarfi. Sai kuma ta sauƙe glass ɗin motar tare da cewa “Haiydar, Ramadan, da Raudat ku shigo motar tunda ku dai ta Ubanmu ne”. Cikin takaici Haiydar ya girgiza kai alamar a'a su tafi. Ita kuwa Khausar ciki takaici ta ɗaga Raudat da Ramadan ta sakasu cikin motar tare da nunawa Haiydar ƙofar motar alamun ya shiga. Murya a cushe yace. “Toh kefa Adda Khausy”. Cikin danne fushinta tace. “Kada ka damu zan shiga Napep”. Zai yi mgn tayi tayi saurin cewa. “Dan Allah kada kace komai shiga kuje”. Ta ƙare mgnar tana turashi ciki, dole ya shiga. Ita kuwa Amina tsaki taja tare da cewa. “Dole su kam shiga ke kuma sai kije can kishiga naki na Uban”. Kallon Habu tayi kana tace. “Haba kaja motar mu tafi”. Da mamaki Habu drive ya kalleta kana yace. “Haba Amina taya zamu tafi mu barta anan dubi hadarin daya taso sannan babu kowa a haraban makarantar ya za'ayi mutafi ne”. Harara ta galla masa kana tace. “Mu tafi kuma wallahi idan ka ƙi na rantse da Allah saina sa Ummah tasa akoreka”. Ahankali Haiydar ya juya ya kalli Amina wanda tun da suka fara magana bai sa baki ba yace. “Haba Addah Amina Meyesa haka Fisabilillah ai koma menene bai kamata ki hanata shiga mota ba dubi hadari fa kuma kin san yadda take tsoron yanayin ruwan sama”. Harara ta watsa masa kana tace. “Rufe min baki an hanata ɗin rufe min baki ɗan Iskan yaro zaka nuna min ƴan Ubanci kenan ruwan ya cinyata, ta mutuma kawai kowa ya huta”. Da ɓacin rai Afuskarsa ya kalleta kana yace. “Ni dai bazan nuna miki ƴan Ubanci ba, saboda bamu tashi da shiba, kuma wallahi idan na koma gida na faɗawa Ummah ma ke kanki kinsan sai tayi miki faɗa”. Dogon tsaki taja tare da cewa. “Kayi sauri kada ƙuda ya rigaka”. Jin haka yasa Haiydar yin shiru sai kuma ya kalli Amina tare da cewa. “Matsa min In ɗauki jakata bazan iya tafiya in barta anan ba”. Girgiza kai Khausar tayi kana tace. “A'a Haidar kada ka ɗauka ka shiga dasu Ramadan ku tafi nima yanzu zan biyo bayanku”. Amina kuwa kallon Habu Driver tayi kana tace. “Mu tafi”. Jin haka yasa Khausar jan marfin motar tare da rufewa kana tace. “Pless dan Allah Haiydar zauna ku tafi, in Sha Allah babu abinda zai sameni”. Dole ya zauba ba don ya soba, Shi kuwa Habu ba yanda ya iya haka yaja motar ya tafi. *Yar uwa littafin SAKAYYAH na kuɗine daga wannan page ɗin na gama Free page, in dai kin ganshi a waje to na satane, a Groups ɗina na sakayya ne ɗai ya halatta, 1k ne biya ki karanta cikin Salamah 0661110170 GTBank AISHA ALIYU GARKUWA ban yafe ba a karanta min littafi ba'a biya ba in kin tura kuɗin ki turo min shaidar biyanki ta WHATSAPP 09097853276* Khausar kuwa shiru tayi tare da bin motar da kallo har ya fice aharabar makarantar, ahankali ta juya ta kalli cikin makantar babu ɗalibi ko ɗaya duk sun watse haka zalika ma Malamai duk sun watse shiru tayi sai kuma ta ɗaga kanta sama ganin yanda hadari ya taso ga iska dake kaɗawa da ƙarfi. Tamkar kazar da ƙwai ya fashewa aciki haka ta fara jan ƙafanta har ta fice acikin Makarantar tsayawa tayi abakin titin koda zata samu Napep amma takai minti biyar babu abin hawan da yazo ya gifta sakamakon hadari daya taso sosai a garin yasa dukkan ababe hawa tsagaita zirga-zirga tana nan tsaye har aka fara ɗan yayyafi hakan yasa ta fara tafiya ahankali a gefen titin. Ba tayi nisa da makarantar ba taji an buɗe gate ɗin makarantar da ɗan sauri ta juya, akan motar Moddibo Idanunta suka sauƙa da sauri ta kawar da kanta gefe kana ta cigaba da tafiya. Acikin mota kuwa Moddibo ne da M Jameel yayin da Moddibo ke Driving M Jameel na gefen me zaman banza. Kallo ɗaya Moddibo yayiwa bayanta ya ganeta, baki ya taɓe Aransa yace yau kuma wannan wani sabon rashin kunya tayi musu suka sauƙeta, sai kuma ya ɗage kafarɗarsa alamun ita ta jiyo. M Jameel kuwa sam bai ganeta ba saida suka gifta wajenta sannan yaga fuskarta. Da mamaki ya furta. “A'a Lelewal”. Cikin sauri ya ɗaura hannunsa kan Moddibo tare da cewa. “A.J tsaya Please dubi duk ɗalibai sun watse amma sai ita kaɗai mai ya tsayar da ita anan kuma ga hadari baƙiƙƙirin dubi fa yanda garin yayi duhu ko Babba hadarin na bashi tsoro yakeyi!”. Juyawa Moddibo yayi tare da Kallonsa cikin yanayin nutsuwarsa yace. “To ina ruwanka da ita!?”. Wara Ido M Jameel yayi kana yace. “Ban gane ina ruwana da ita ba? ɗalibarmu cefa! sannan kullum a mota ake kawo su sannan zuwa ake aɗauke su, kana mun ganta ba'a tafi da ita ba sannan ka duba ita kaɗai ce a layin nan dubi fa yanda layin babu kowa”. Kallon gefen Ido Moddibo yayi masa kana ya taɓe baki. Da sauri M Jameel ya cigaba da cewa. “Haba A.J ya za'ayi kace haka?”. Moddibo kuwa juya idanunsa yayi kana yace. “Toh Meye haɗin mu da ita? kasan Meye Uzurin daya tsayar da ita? Sannan kasan Meye dalilin tsayuwarta! Wata ƙil ma wani bishiyoyin anguwar takeson hawa”. Girgiza kai M Jameel Yayi kana yace. “Ai koma mene sai mu tsaya mu tambayeta ko?”. Kallonsa Moddibo yayi kana yace. “Nifa bazan tsaya ba”. Langwaɓar da kai M Jameel yayi kana cikin sanyin murya yace. “Dan Allah A.J da darajar Annabi Muhammad (S.A.W) mu taimaki yarinyar nan. Yanzu idan Asma'u ce zaka iya barin ta awajen nan ne?”. Da sauri Moddibo ya kallesa kana yace. “Asma'u kuma mai ma zai tsayar da ita anan mai zai haɗa ta faɗa da wasu har tayi musu rashin kunya su sauƙeta amota, ai Asma'u baza ta kasance haka bama!”. Sake Langwaɓar da kai M Jameel yayi kana yace. “Amma kayi tunani ƴa mace ce ita ko addininmu ya koyar mana da kula dasu da kuma kula da al'amuran daya shafesu A.J bai kamata ba na roƙe ka dan Allah ba danni ba kuma badan ita ba dan Allah da kuma darajar Manzon mu kayi haƙuri ka tsaya! In ma bazaka ɗauketa ba, ni ka sauƙin bazan iya tafiya in bar Khausy cikin wannan yanayin A.J bazan iya barin ta ananba”. Ya ƙarashe mgnar cikin wata iriyar raunatacciyar murya mai fito da sirrin dake binne cikin zuciyarsa. Hannu Moddibo ya sanya tare da dafe goshinsa alamar ya gaji da damuwar M Jameel ahankali yasanya lallausan tafin hannunsa ya shafa sajensa ba tare da yace komai ba ya taka burki ya tsaya. Yana mai kallon yadda M Jameel ya sauƙe numfashi. Ganin ya tsaya ya sanya M Jameel sakin murmushi tare da buɗe motar ya fita cikin sassarfa da ɗan gudu ya nufi inda Khausar take dan sun ɗanyi mata nisa kana ga yayyafin da aka fara da ƙarfi da kuma rugugi alamar ana gaba da kecewa da ruwa mai ƙarfi. Moddibo kuwa da kallo yabi M Jameel ta mirror motarsa. Aransa yace Ohhh J ji yanda yake gudu kamar wani yaro ko ya gani a wannan ƴar nan har yake jinta cikin zuciyarsa. Khausar kuwa tana ganin M Jameel ta saki nannauyan Ajiyar zuciya tare da cewa. “Yaya Jameel”. Cike da kulawa ya kalleta tare da cewa. “Lelewal mai yafaru yana ganki anan ke kaɗai, bayan baki ɗaya student's sun watse”. Ahankali ta kallesa sai kuma tayi saurin lumshe Idanunta tare da cewa. “Wallahi Yaya Jameel Amina ce ta hanani shiga motarsu yau kam masifa take ji dashi”. Girgiza kai yayi tare da faɗin. “Subhanallah gaskiya bata kyauta ba, maza zo ki shigo mota mutafi”. “Toh”,tace tare da bin bayansa cikin sassarfa yayinda ko wanne gaɓa na jikinta ke motsawa. Ɗan guntun tsaki Modibbo yaja, tare da kauda kansa daga kan madubin, ganin yadda suka wani jero da J ɗinsa. Suna isa wajen motar M Jameel ya buɗe mata bayan gefen da Modibbo yake tashiga, sannan shi kuma ya zagaya ya shiga a hankali Khausar ta ɗaga kanta tare da kallon gaban motar ai kuwa idanunta suka sauƙa akan Moddibo da batasan yana cikin motar Ba gashi ta zauna asaitin bayansa. A kuma dai-dai lokaci ruwa ya kece tamkar da bakin ƙorya, key Moddibo yayi wa motar tare da figarta a dan guje suka fara tafiya. Kallon Moddibo M Jameel yayi kana yace. “A.J kasan zamu biya ta gida ka sauƙe ni tun safe Abba ke kirana wai Inje Yana son magana dani muje ka sauƙe ni”. Kallon sa Moddibo yayi tare da cewa. “Baza ka bari sai anjima ba?”. Girgiza kai M Jameel Yayi kana yace. “A'a muje dan Allah ka sauƙe ni saboda bansan me yake sona dashi ba yanata ne mana tun tuntuni”. Kai Moddibo ya gyaɗa kana yace. “Toh naji”. Yayi mgnar tare da haharan M Jameel ɗin, Sannan ya cigaba da Driving ɗin sa. Shi kuwa M Jameel murmushin yayi tare da ɗan mishi alamun zunɗe. *Littafin SAKAYYAH na kuɗine daga wannan page ɗin na gama Free page, daga gobe in dai kinga littafin SAKAYYAH a wani wuri to na satane, yar uwa ki biya 1k ne kacal ki karanta cikin Aminci ba haƙƙin kowa a kanki littafin SAKAYYAH na kuɗine ƴar uwa kada ki karanta in baki biyaba 0661110170 GTBank AISHA ALIYU GARKUWA, sai ki turo min shaidar biyanki ta WHATSAPP 09097853276* Khausar dake zaune abayan motar kuwa ƙanƙame jikinta tayi saboda yanda ɗumin motar ke ratsata sam cikin motar babu sanyi da yawa ba kamar waje da iska ke kaɗawa ba. Sanyayyar Ajiyar zuciya ta sauƙe tare da gyara Questions peper dake hannunta ta sake rungumesu aƙirji sai kuma ta gyara zaman wuyan hijabinta wanda har tattausan gashin gaban goshinta mai sansti ya bayyana. Baki ɗaya cikin motar a wadace yake da wani irin ni'imtaccen sanyayyan ƙamshi mai daɗin shaƙa yakeyi, Ahankali Khausar ta maida kallon kan bayan Moddibo da take fuskanta sanye yake cikin ɗanyen Boyel fari ƙal yasha guga sosai yayin da kansa ke sanye da hula zanna bukar wadataccen sumar ƙeyansa ya kwanto lib-lib gwanin kyau sai sheƙi da ƙyalli yake zubawa. Ƙeyar tasa ta zubawa ido sai kuma ta gallawa ƙeyar tasa harara tare da murguɗa masa baki. Tana ɗago Idanunta suka sauƙa akan Idanun Moddibo ta madubin jikin motar yana kallonta cikin mugun sauri tayi ƙasa da kanta zuciyar ta na mai bugawa da ƙarfin tsiya. Moddibo kuwa Ƙoffa yayi tare da haɗa harshensa da hoƙorinsa ya fitar da wani sauti kana yace. “Hmmmm!”. Kallon sa M Jameel da Idanunsa ke lumshe yayi kana cike da kulawa yace. “Ya dai A.J?”. Shiru Moddibo ya masa tare da watsa masa Harara!. Ware Ido M Jameel yayi tare da shafa sajensa kana yace. “Ya dai kake ta harare-harare acikin mota!”. Ƙin tanka masa Moddibo yayi ya cigaba da Driving ɗinsa tare da ƙara tsuke fuska. Khausar kuwa shiru tayi sai kuma ta sake ɗago kanta ahankali ta kalli madubin ganin ya kawar da kansa gefe yasa ta sake liƙawa ƙeyansa harara tamkar idanunta zasu manne bisa ƙeyar tasa, kana ta ɗago hannunta na dama ta ɗan haɗe kan yatsun tare da buɗe su ta watsa masa alamar Jarabebbe! Mayatacce!! Masifeffe!!! Fitinenne!!!! sai kuma ta sake watsa masa Harara tare da kai hannunta ƙeyarsa kamar zata kai masa ronƙwashi. A kuma dai-dai lokacin ya ɗago ya kalleta ta madubin. Azabure taja baya tare da jinginar da bayanta da jikin kujeran zuciyarta na bugawa. Cikin fushi Moddibo ya watsa mata mugun kallo tare da cewa. “Anh zan karyaki wallahi kakkarya ki zanyi in watsar dake atiti inyi tafiyata, ƴar rashin kunya fitsararriya”. Ita dai Khausar rumtse Idanunta tayi da masifan ƙarfi tare da sake rungume question peper ta aƙirji gam-gam. M Jameel kuwa daya ta kure jikinsa waje ɗaya idanunsa alumshe saboda sanyi da ake yayi saurin buɗe idanunsa yayi tare da kallon Moddibo dake Driving tamkar bashi yayi maganar ba cikin tsaresa da Ido yace. “Ha'a wai mai yake faruwa a motar nan ne kake abubuwa iri-iri daga Harara, Ƙoffa, tsaki, tsuke fuska, yanzu kuma sai cewa zaka kakkarya!,To waima wa zaka karya ne kam?”. Cikin fushi Moddibo ya juya ya kallesa kana yace. “Ai duk wanda zan karya ya sani! Karya yarinyar nan zanyi fitsararriyar banza mara kunya idan kina sake kuskuren kallon min ƙeyata saina gutsitsi-tsiraki na ƙwaƙule miki manyan mayatattun idonun ki masu kama da na yan maye na jefar! A titi ko na samu salama”. Lokaci ɗaya tsoro ya dirarwa Khausar jin wai zai Kakkarya ta ya ƙwaƙule mata ido cike da tsoro ta kuma ƙara rumtse Idanunta tare da ta kure jikinta ajikin kujera ita kanta batasan dalilin da yasa yake mata haka ba ita dai tasan da zata samu dama itama karyashin zatayi ta kuna tsitstsige gemunshi. Akuma dai-dai lokacin suka isa ƙofar gidan su M Jameel Moddibo yayi Parking. Ɓude Murfin motar M Jameel yayi tare da fita duk da ruwan da ake tsugawa bai hana sa saka kansa ta cikin glass ɗin side da Khausar take ba, cikin ƙasa da murya yace. “Lelewal be careful don't Misbehaving kinga bana nan yaseen kika mishi ba dai-dai a titi zai wurgaki ya tafiyarsa”. Kai ta gyaɗa masa cike da alamun tsoro sai taji kamar ta fita ta bisa. Shikuwa M Jameel kallon Moddibo yayi tare da cewa. “Toh Allah ya tsare Allah ya kaiku lafiya A.J Amana ce, dan amana A.J ka kularmin da ita”. Daga haka ya juya da gudu ya nufi cikin gida zuwa lokacin duk ya jiƙe saboda yanda ruwan ke sauƙa da ƙarfi. Acikin motar kuwa lumshe idanu Moddibo yayi ba tare da yaja motar ba. Khausar kam ƙasa da kanta tayi aranta tace wannan dai akwai bahagon mutum, fisabilillah yana kallon yanda ake tsuga ruwa kamar da bakin ƙwarya amma yaja ya tsaya jifa yanda ruwan ke sauƙa. *Littafin SAKAYYAH na kuɗine daga wannan na gama Free page, 1k ne kuɗin samun damar karantawa 0661110170 GTBank AISHA ALIYU GARKUWA, biya ki karanta cikin Aminci* Sun kai kusan minti biyar ahaka ita batace komai ba, haka zalika shima baice komai ba banda sautin ƙaran ruwa babu abinda ke sauƙa ɗago Idanunsa yayi dai-dai lokacin da itama Khausar ta ɗago Idanunta ta kalli madubin cikin motar, idanunsu ne suka sarƙafe cikin na juna. Harara ya watsa mata kana cikin wata razananniyar murya da shi kansa bai san yana da ita ba yace. “Uban me kike abayan mota koni. Driver kine harda wani hakimcewar ki abaya a dole kega Sarauniya kin samu Driver! Kifita idona fa, nifa ba J bane zan karya kifa”. Cikin sauri ta buɗe bayan motar ta fita aranta tace Gwanda inyi yanda yake so dan yanda yake kiran zai karya nin nan inda yazo da tsautsayi sai yajawa Mommy asarata, gaban motar ta buɗe ta shiga amma duk da haka saida ta ɗan jiƙe sabida ruwan da ya fara ƙarfi, tana zama yaja motar suka tafi. Akuma dai-dai lokacin ruwan ya sake kecewa da ƙarfin gaske tamkar da bakin ƙwarya ake tsuga ruwan. Khausar kam lumshe Idanunta tayi aranta tace ya Allah ka kaimu gida lafiya ka rabani da wannan bawa naka lafiya, domin akwai rata tsakaninsu da gida sosai ahankali ta buɗe Idanunta ta kalli titin da yayi shiru babu hayaniyar sai ƙugin motarsu da kuma yanda tayun ke fesar da Iska da ruwan kan kwalta fuuuu kana har zuwa yanzu garin ɓakiƙƙirin yake duk da kuwa yadda ake sheƙa ruwan alamar har yanzu ruwan bashi da niyyar ɗauke wa. Suna cikin tafiya akayi wani irin walƙiya mai haske. Da sauri Khausar ta rumtse idonta tare da furta. “Bismillahi”. A lokacin guda kuma ta sake buɗesu da sauri sabida jin wani irin rugugi da akayi mai bada sautin rududuuu-duuuuhhh kana ga walƙiya daya haska da wani irin sauri Khausar ta rungume jikinta waje ɗaya aranta tace. _“Innalillahi wa'inna ilahi rajiu'n Hasbunallahu wani'imal wakil Subhanal Lazi yusabbihul ra'adu bi handihi wal Mala'ikatu min hiyfatin”._ Cikin tsananin tsoro tayi addu'ar domin arayuwarta babu abinda take masifar tsoro a damuna kamar tsawa da walƙiya sam bata yarda ta haɗa ido da walƙiya da zaran taga za'a yi walƙiya zata rufe Idanunta ta sunkuyar da kanta. Shi kuwa Moddibo tafiya ya cigaba dayi yayin da titin yayi shiru babu hayaniyar komai sai bishiyoyi dake rangaji ruwa na sauƙa akansu Sanyayyar iska mai cike da Ni'imah na kaɗasu baki ɗaya shaguna dake gefen titin arufe suke baki daya garin babu hayaniya sai jefi-jefi suke hango Mutane. Suna cikin tafiyar aka sake wani walƙiya mai masifar haske ja, alamun yanzu za'a ƙara kecewa da ruwa. Atsorace cikin ɗaga sautin murya tace. “Innalillahi wa'inna ilahi rajiu'n”. Ta ida addu'ar tare da kife kanta akan gwiwarta yayin da gaba ɗaya ilahirin jikinta ke rawa A ɗan juya kai Moddibo yayi kalleta, domin shi kansa zuciyarsa ta harba sabida walƙiyar saida ta ɗauke masa ido saboda yanda walƙiyar tazo da haske mai ƙarfin gaske sosai yaji tsoron walƙiyar amma sai yayi addu'a aransa kana yana cigaba da tafiya bai tsaya ba. Bayan walƙiyar ba daɗewa aka saki wata tsawa mai sautin rututuuuu alokaci ɗaya zuciyarsu ta buga domin ji sukayi tamkar ƙasa zai tsage. Atake wani matsananci tsoro ya sake lulluɓe Khausar yayin da jikinta yashiga rawa tamkar mazari kanta ta kife acinyarta zuciyarta na cigaba da bugawa da masifan ƙarfi kana har zuwa lokacin kanta na sunkuye akan ƙafafunta tun daga wannan rugugin. Yayinda gaba ɗaya mazauna garin Gembu Mebila suke cike da taraddadi sabida bisa dukkan alamu yau da tsawa da rugugin ruwan yake sauƙa. Acikin haka ne aka sake walƙiya mai masifar haske irin walkiyar nan mai zuwa tamkar an watsa dogon bulala koko tafiyar maciji, Da masifar haske da tarsatsi yazo tamkar an watsa bulala Sharrrrrr sai kuma a take aka saki wata iriyar tsawa mai masifar ƙarfi yabi yo bayansa wanda ke fitar da sautin felelelelelelelen da masifar karaji da gigita dukkan bani adam Cikin wani irin tsananin tsoro da gigita Khausar ta saki ƙara mai masifar sauti tare da furta. _“Hasbunallahu wani'imal wakil. Subhanal Lazi yusabbihul ra'adu bi hamdihi wal Mala'ikatu min hiyfatihi”._ Atake aka sake sakin wani walƙiyar haɗe da wata iriyar firgitacciyar tsawa mai masifar kara mai razana dan adam dasa hanjin mutum kaɗawa. Cikin tsananin tsoro da masifar gigita ta dari ta ɗago kanta a kiɗime ta afkawa jikin Moddibo yayin da gaba ɗaya ilahirin jikinta ke rawa shi kansa Moddibo wani irin tsoro ne ya kamasa saboda hasken walƙiyar saida ya tsaga glass ɗin gaban motarsa tare da bada sautin ƙarararassss!!!. Wani irin bugawa zuciyarsa keyi da masifar ƙarfe yayin da gaba ɗaya ilahirin jikinsa ya ɗauki rawa ƙoƙarin taka burki yake amma ya gagara saboda yanda ta takure jikinta ajikinsa ta kanainayeshi, bashida wani kataɓus ɗin motsa wa, sabida yadda ta kife kanta afaffaɗan ƙirjinsa hannunta ɗaya na zagaye da bayansa yayin da ta cusa hannunta na dama akan maransa. Moddibo kuwa wani irin masifaffen rawa jikinsa ya farayi tamkar mazari yana wani irin tsuma ji yake tamkar ana tsikara masa allurai ne agaba ɗaya ilahirin jikinsa lokaci ɗaya wani irin baƙon yanayi ya ziyarcesa ga fargaban tsawar da har zuwa lokacin bai gama tsayawa ba. Tsawan na tsayawa wani mai masifar rugugi ya sake sauƙa. Wani irin masifaffen tsuma jikin Khausar keyi yayin da numfashinta ke fusga saboda tsananin tsoro Allah ya sani tana masifar tsoton tsawa hakan yasa ta sake ƙanƙamesa tamkar zata tsaga jikinsa ta shige ciki. Shi kuwa Moddibo baki ɗaya jikinsa tsuma ya shiga yi saboda yanda ta kanainayesa kar-kar-kar haka jikinsa ke rawa yayin da baki ɗaya tsikar jikinsa ya miƙe daga tsakiyar kansa har zuwa babban yatsan ƙafarsa yaji wani irin yanayi wanda bai taɓa jiba a iya tsawon rayuwarsa, sai yau kuma yanzu ya jishi. Wani irin harba zuyarsa da sashi mafi daraja a jikinsa sukayi a tare da wani irin azaban ƙarfi. Akuma lokacin aka sake sakin tsawa da walƙiya. Ita kam Khausar cikin tsananin gigita da tsananin tsoro kana da ficewar hayyaci ta sake rungumesu tare da sake tura hannunta ka maransa yayin da yatsun hannunta suka sauƙa akan cibiyar sa. Tsawar da aka sake yine ya razana illahirin wani abu mai rai dake yankin Gembu, yayinda hakan take a wurin Modibbo ma wani cikin rashin sanin makaman kamawa ya ya buɗe hannayensa ya rungumeta da azaban karfi tare da taka burkin motar da ƙarfi wani irin sautin ƙuuuuuuu motar tayi tare da cigaba da tafiya sabida tsantsin kwaltan da yayi sabida ruwan sama da kuma tsantsin sabbin tayoyin da ƙyar ya samu motar ta tsaya a tsakiyar titin, sake Rungumeta yayi da masifar ƙarfe kana ya cusa kansa atsakanin kafaɗarta da wuyanta. Lokacin da aka kuma sakin wani irin rugugin nan da zakaji kamar ƙasa na amsawa. Atake zuciyarsu ya buga da mugun ƙarfi tare da bada sautin dib-dab-dib-dab-difffh yayin da yake jin wani irin masifaffen abu na tsirgar masa lokaci ɗaya lafiyarsa sa ta shaida mushi kasantuwarsa cikekken Namiji. Ita kuwa khausar tana jin yatsarta cikin ɗan hudan cibiyarsa amma tsananin tsoron da take ciki yasa ta kasa fahimtar menene sai cusa kanta da ta kumayi a kirjinsa. Shi kam Moddibo wani irin rungumeta yayi da masifar ƙarfi yana mai sakin wani irin amintaccen nish....! *Free page sun ƙare daga wannan, ko kin ga littafin a wani wuri na satane, littafin SAKAYYAH na kuɗine 1k ne 0661110170 GTBank AISHA ALIYU GARKUWA sai ki turo min shaidar biyanki ta WHATSAPP 09097853276. Sai in saki a Group ɗin da nan kadai zanke posting* *WOHOHO IN KAJI ANA ƘI GUDU TABBAS SA GUDU NE BEZO BA* _Ina kuke Ma'aurata masu sha'awar ganin sun zama taurari kuma fitilu a idanun mazajensu Uwar gida,Amarya,Tsakar gida,hadda tan kaɗen gida Shararriya kuma ƙasaitacciya data saba kawo muku nau'ikan sirrin sahihan magungunan ma'aurata wato *AYSHA ALIYU GARKUWA* Garkuwar Marubuta ayau ma ta dawo muku da Ingantattun magungunan mata masu kyau da inganci domin gyara kanki ki zamto tauraruwa a idanun mijinki...Muna da Ingantattun Abubuwa kamar haka_ :_Munada Garin mallaka, garin maɗi, garin Hakkin mayi, garin ɓelɗamhi Garin ilanwaddihi, Gumbar da ba'a baiwa mai kishiya, Gumbar kolli mai kellin al'khairi, Gumbar Riɗi wato 3 in 1, Gumbar makwaranyi, Masin Maliƙi mai masifar ƙarfi da matse mace, ka masin Daɗi har Maɗigan Akwai, kwanon ƙasaitacciyar mace mai masifar kyau da ratsa jiki da samar da inƙantacciyar ni'ima yanada abubuwa masu kyau haɗinsa, Zumar goron tula mai masifar kyau, tsumin dabino, mai ratsa jiki, tsumin Riɗi mai ƙarfi, Furar Mata mai tsastsafo da ni'imantaccen damshi, Cida kaza, Ciccibi Abodi, Tsumin Ɓaure, tuwon ɓauren, kana akwai maganin sanyi sadidan, da dai sauransu...Se kuma fannin ƙamshi kasance da Shu'umin ƙamshi wanda ze gigita ƙwaƙwalwar Oga tare da jin ko wacce mace bata kaiba...._ _Shin ko kina da labarin Miskilinci da ƙasaitar Rayyan Naaan amma lokaci ɗaya ya zamto zautacce sakali akan soyayyar Jannart bakomai Jannart ta riƙe ba face sirrinkan gyara da kuma shu'uman humran da kulaccar sirri na Aysha Aliyu Garkuwa(Tubali) tabbas taga tasirin haka domin Naanunta ya zame mata tamkar bawa_ _Shin ko kinsan sihirtaccen haɗin da Aysha ke sha kenan ta zamto tauraruwa a idanun Hamma Yusuf(Miwasmiti)...Tabbas Mahmud ya zamto zautacce kuma makaho akan sauyayyar Bazawara wato khadijarsa duk da kuwa gashi da budurwa(Namiji Baya Kaɗan) ko kinsan hakan nada alaƙa da amfani da sahihan maganin da kuma shu'uman humran Aysha Aliyu Garkuwa??.Nasan ba zaka ku manta da irin kima da kuma darajar da Aysha ke dashi acikin Idanun Sheik Jabeer ɗin ta duk da kuwa shekaru sunja anma jinta yake tamkar budurwa 'yar sha bakwai(Garkuwa) sirrin hakan na tare da Ingantattun kuma sahihan magungunan Aysha Aliyu Garkuwa Wato Garkuwar Marubuta da kuma Ma'aurata na tabbata kunsan da cewa basirarta ba'a iya rubutun littafi ya tsaya ba hadda inganta rayuwar ma'aurata ta hanyar kawo musu Nagartattun abubuwa Ga duk wacce ta shirya saya seta tuntuɓi number ta 09097853276 muna iya tura kayan mu aduk inda kuke afaɗin Nigeria harma da ƙetare Dan Allah 'yar uwa idan baki shirya siyaba kada kiyi min magana muɓatawa kanmu lokaci...._ 🤝🏻🤝🏻🤝🏻🤝🏻🥰😘sai.kunzo. sayan na gari maida kuɗi gida, *By* *GARKUWAN MARUBUTA* [24/07, 6:14 AM] Halimatu A/rahman Sadeeya: SAKAYAH 18 🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇 Spjt. Rungume juna sukayu tamkar zasu shige cikin jikin junansu, yayin da ruwan sama kuwa ke cigaba da sauƙa tamkar da bakin ƙwarya, kana ga walƙiya da tsawa dake cigaba da sauƙa. Moddibo shi kam baki ɗaya ya burkice ya rasa tunaninsa, na wushin gadi, gaba ɗaya jinshi yake a wata duniya ta da ban, ga wani matsanancin tsoro daya lulluɓe sa kana ga wani baƙon yanayi da yake ji yana yawo agaba ɗaya ilahirin ajikinsa, wani irin rawa lips ɗin sa keyi tamkar mai jin tsananin sanyi, ga kuma wani irin azabebben buguwan da zuciyarsa keyi da masifaffen ƙarfi yana bada sautin dib-dab-dib-dab. Haka zalika Khausar dake rungume dashi, itama haka zuciyarta ke bugawa, sake ƙanƙamesa tayi da ƙarfi tana mai tura kanta afaffaɗan ƙirjinsa da bottle din gaban rigar suka buɗe, hakan ya bawa fuskarta damar mannewa farar afaffaɗan ƙirjinsa dake ƙawace da tattausan gashi baƙi mai sulɓi. Wani irin fusga numfashinta keyi saboda tsananin tsoro da firgici da tashin hankali, haka yasa idan taja numfashin sai ta ɗauki sekon talatin Kafin ya dawo. Ko kaɗan Moddibo bai da wani kataɓus sabida yanayin da suka kasance a ciki, sake rungumeta yayi tare da cusa kansa atsakanin wuyanta da kafaɗarta. Daga can bayansa yake jiyo sautin ƙaran mota tana danna masa ɗiyyyyttt-ɗiyyyytttt, yasan shi akeyiwa hon ɗin, amman sam baya jin zai iya koda kwakwaran motsine. Shi kuwa mai motar dake bayansa, ganin shiru bai motsa bane, yasa ya ɗan ratsa ta gefensu ya fuce yana dan leƙawa ganin ko lafiya kasancewar. Atsakiyar titin suke ganin babu wani alamun hatsari ko damuwa yasa ya wuce. Moddibo kuwa da ƙyar ya iya buɗe Idanunsa tare da ɗago kansa still ruwan ake sheƙawa zuwa yanzu harda ƙanƙara yana jin yanda sautin ƙanƙarar ke sauka asaman motarsa fat-fat-fat ko kaɗan baya kallon komai duk da kuwa gashi idanunnasa abuɗe suke, amman ina ganinsa ya ɗauke makanta ta meye gurbin ganinsa, ya zama sam baya gani, kana ji yake jikinsa kamar shanyeyye. Daƙyar ya iya ɗaga hannunsa tare da dafe kansa da yake jin wani irin jiri na fizgarsa tare da sarawa, da sauri ya sake sunkuyar da kansa akan wuyanta kana ya sake rungumeta da ƙarfi baki ɗaya ya rasa wani irin yanayi yake ciki. Khausar kam sam batama san wani irin yanayi take ciki ba sam bata cikin hayyacinsa, hakan yasa ta sake rungume Moddibo da ƙarfi, Jin yadda take liƙewa a jikinsa ne, yasa shima ya saƙe yi mata wani irin amintaccen rugguma tare da fesar da wani irin raunataccen numfashin yana mai shaƙan ƙamshin jikinta. Itama sake rungumesa tayi cikin mawuyacin hali tana neman numfashi domin numfashinta na ƙoƙarin ɗauke wa gaba daya tsananin tsoro da tashin hankali ya bayyana asaman fuskarta, duk da sanyi garin da kuma yanda ake tsuga ruwa amma goshinta na na tsastsafo da zufa kana jikinta ya ɗauki ɗumi. Cikin wani irin yanayi mai wuyar fassarawa da ficewar hayyaci Moddibo ya sake rungumeta yana jin ɗumin jikinta kana yana mai furta. “Hasbullahu wani'imal wakin, Innalillahi wa'inna ilahi rajiu'n La'ilaha Illah anta subhanaka Inni ukuntu Minal Zhalimin, Allahumma Ajirni fii musibati wa'ahlifli khairan minha”,Kana ya cigaba da karo to duk wata addu'a da tazo bakinsa cikin fitar hayyaci, Allah ya sani kuma shine shaidarsa ya rasa yanayin da yake ciki shin mutuwa zaiyi ne, koko kuma sumewa yake shirin yi, domin jinsa yakeyi tamkar yana tafiya cikin sararin samaniya ne bisa gajumare, ji yake tamkar fuka-fuki garesa ya kasa tantance shin mafarki yake ko kuma azahirance ne kana yakasa tantance shin a sumen yake ko kuma amace yake, cikin rashin sanin madafa ya cigaba da karanto duk wata addu'a da tazo bakinsa. Yayin da numfashi Khausar ke cigaba da fusga, adduo'i ya cigaba dayi cikin ikon Allah Albarkanci Adduo'i da yake da kuma zuciyar namiji dake da dakiya yasa yafara dawowa hayyacinsa amma still Idanunsa basa gani mai kyau. Ganinta kwance ajikinsa tana fuzgar numfashi yasanya shi sa. Lallausan tafin hannunsa ya tallabo fuskarta tare buɗe manyan idanunsa da ƙyar dan har yanzu dishi-dushi yake gani, idanu ya tsirawa kan goshinta daya tsats-tsafo da zufa, sai kuma ya rumtse idanun da karfi kana ya buɗesu tare da zura ido na daƙiƙu bakwai sai kuma ya juya idanun zuwa kan wuyan hijabinta daya zame daga kanta zuwa kafaɗarta yalwataccen sumar kanta mai tsayi da ƙamshi ya zuba agadon bayanta, yayinda saura kuma ya zuba asaman fuskarta, kallonsa ya mayar kan fuskarta jin, yanda numfashinta ke fusga. Idanunsa ya mayar kan ƙirjinta da sauri ya lumshe idanun sai kuma ya buɗesu, ganin yanda numfashinta ke hawa da sauka alamun zata sume a ko wanne lokacin. Ganin tana gab da sumewane ya sanyashi sun kuyar da kansa kaɗan, zuwa kan fuskarta kana ya ɗaura lips ɗin da suke masifar rawan sanyi akan karan hancinta, lumshe manyan idanunsa da suka sauya launi zuwa ja yayi, tare da fesa mata sanyayyan numfashinsa domin dai-dai ta mata nata numfashin, domin duk da tsoron da kuma firgicin da yake ciki hakan, bai sanya numfashinsa ɗauke wa ba, kana yana kallon fuskarta wanda akowani lokaci zata iya suma, sai kuma ya sanya hannu ya toshe hancinta tare da ɗaura sanyayyan lips ɗin sa akan nata ya riƙa hura mata iskar bakinsa mai ɗumi da kamshi ceto rayuwa zuwa gareta, Wani irin dogon numfashi taja mai nauyi tare da fesar dashi da ƙarfi, cikin daƙiƙu kaɗan numfashinta ya soma dawowa dai-dai kana duk abinda ke faruwa idanunta na lumshe. Sannan har zuwa lokacin hannunta na kan mararsa, saman yatsarta na kan hudan cibiyarsa, sannu ahankali numfashinta ya dai-dai ta sai dai har zuwa lokacin bata dawo hayyacinta ba, still kuma ruwan ake cigaba dayi tamkar da bakin ƙwarya ita ko sai wani irin sakewa tayi tare da lafewa a jikinsa tana shaƙar ƙamshinsa. Shi kuwa Moddibo sannu ahankali ya fara dawowa hayyacinsa da nitsuwarsa. Sake lafewa Khausar tayi ajikinsa tare da lumshe Idanunta domin ganin abun take kamar mafarki, ko kuma mutuwa tayi tsaban masifar tsoron rugugin da take. Shi kuwa Moddibo sannu ahankali cikin ikon Allah ya dawo hayyacinsa, kana har zuwa yanzu tsikar jikinsa na tashi yayin da kansa ke juyawa jiri na ɗibarsa. Ahankali ya sauƙe idanunsa akanta data manna a ƙirjinsa, yayinda tattausan suman kanta ya baje aƙirjinsa, kallonta yakeyi kamar ya samu sabuwar halitta, kana aƙasan ransa ke mgnar zuci, Wai yaya haka ne? Mekw faruwa? Wai ma waye ni? Ya tambayi kansa da kansa, Kaine Moddibo, sannan wannan Khausar ce kwance ajikika tana rungume dakai cikin yanayin da ma'aurata ne kaɗai ya halatta su kasance ciki. Wani sashi na zuciyarsa ya bashi amsa. Lokaci ɗaya kuma jikinsa ya sake ɗaukar rawa far-far tamkar wanda ake sheƙa masa ruwan ƙanƙara lips inshi kuwa, wani irin masifeffen tsuma sukeyi, lumshe idanunsa yayi jin jikinsa babu kuzari kona misƙala zarratin, ji yake tamkar an zare masa lakar jikinsa cikin sanyi da rashin kuzari dake tare dashi. A hankali ya sake birkitota tare da ɗago kanta ya ɓanɓareta daga jikinsa gani yayi Idanunta alumshe. Ita kuwa Khausar ji take tamkar cikin bacci take, ko kuma suma ta kasa fahimtar kalar yanayin da dai take ciki, Shi kuwa Modibbo kanta ya tallabe da hannunsa ɗaya yayin da ɗaya hannu yake ɗan marin fuskar yana faɗin. “Ke! Keh!!”. Shiru bata motsaba, hakan yasa ya sake ɗan fizgo muryasa tare da faɗin. “Khausar! Khausar!!”. har zuwa lokacin tana rungume jikinsa For the first time arayuwarsa da bakinsa yafara kiran sunanta. Fuskarta yake ɗan yiwa ƙananan maruka ahankali kana cikin wata Sanyayyar murya mai cike da tattausan lafazin yake fadin. “Khausar!, Khausar!! Khausaaaar!!!”. Lumshe idanunsa yayi shi kansa bai san yana da irin wannan raunataccen muryar ba, ya rasa taƙamemmen yana yin da yake ciki, yayin da aƙasan ransa so yake ya mata faɗa da tsawa da masifar ta sauƙa jikinsa, amma ya kasa kasancewar har zuwa lokacin bai gama dawowa cikin ainihin nutsuwarsa ba. Kumatunta ya cigaba da ɗan mara yana faɗin. “Khausar!, Khausar!!”. A hankali kanta ya zame daga hannunsa ya tafi gefe luuuh kamar sumammiya. Lokaci ɗaya zuciyarsa ta buga da ƙarfin gaske tare da jin tsinkewar zuciya ganin yanda Kanta yayi kamar ta mutu!. Cikin ɗaga sautin murya ya sake ɗan marin kuncinta tare da cewa. “Khausar, *Lelewal*”. Khausar kuwa still Idanunta na lumshe take Jin sautin muryar Moddibo na kiran sunanta kamar amafarki ko kuma daga can sama. Sai kuma ta sake jiyo sautin muryarsa da alamun kiɗima yake cewa. “Ya salam Lelewal meya faru? me ya sameki?”. Ahankali ya sanya hannunsa tare da ture hijabinta kana ya sanya hannunsa aƙirjinta wanda har yana iya jin tudun caɓɓullen ta ahannunsa ji yayi ƙirjinta na bugawa da ƙarfi-ƙarfi. Hannunsa ya cire tare da sunkuyar da kansa har suna shaƙar numfashi bakin juna, bakishin yakai kan kunnenta kamar meyu mata raɗa yake faɗin. “Lelewal tashi! Lelewal buɗe idonki!! Lelewal kalleni”. Lumshe Idanunsa yayi akaro na barkatai tare da kai bakinsa cikin kunnenta kana cikin Sanyayyar murya mai taushi yace. *“Fattanah!”.* Dogon numfashi taja tare da sauƙe nan-nauyan ajiyar zuciya tare da buɗe Idanunta sai kuma ta sake runtsesu da sauri gani take tamkar har yanzu rugugin akeyi kana walƙiyar zai iya kashe mata Idanu. Bayan kamar daƙiƙa ɗaya ta sake buɗe Idanunta still yana ronƙofe akanta yana shaƙar ƙamshin numfashin dana gashinta dake baje. Yayin da har zuwa yanzu hannunta ke cikin sa yatsunta guda uku nakan cibiyarsa tafin hannunta da sauran yatsu biyun nakan ainihin mararsa ta danne. Cikin wata sanyayyar murya ya tsira mata idanu tare da faɗin. “Lelewal”,Ya faɗa still yana tallafe da kanta. Buɗe Idanunta tayi sai kuma ta sake rufewa, Akuma dai-dai lokacin Moddibo da itan duk suka gama dawowa cikin hayyacinsu tare da nutsuwar. Cikin sauri tare da fushi Moddibo ya kalleta a tsawace yace. “Keee!!! Tafi can Mage uwar fitina tashi akaina ko in kakkaryaki”. Ya dire mgnar cike da tsawa tare da yarfa mata mari da bayan hannunsa. Shi kansa jin maganar yayi ta fito daga zuciyarsa kai tsaye kamar an fisgo a bakinsa. Azabure Khausar ta buɗe Idanunta dake lumshe tare da janye jikinta daga nasa amma still hannunta na kan cikinsa tana murza cibiyarsa. Wani mugun kallo mai cike tarin kufula, takaici, tsuyan zuciya, da tarin ƙunci ya watsa mata firgitaccen kallo. Ta da ɗaga hannunsa cikin wani irin masifeffen rawan jiki da gigitan yanayi yasanya tafin hannunsa ya finciko hannunta dake kan cikin sa da masifar ƙarfi ya yarfa hannun nata har saida ta saki ƙara, dan ji tayi kamar zai ɓalla mata hannun. Shi kuwa a take kuma tsikar jikinsa ta mimmiki ta tashi. Cikin tsananin tsoro da firgici Khausar ta janye jikinta kana ta koma ta mannu da jikin kujera tare da rungume kanta a can gefen jikin kujeran motar tana mai jin raɗaɗin marin. Moddibo kuwa da ƙarfi ya rumtse idanunsa sabida wani irin masifaffen har bawa da yaji zuciysrsa nayi da masifar ƙarfi, lokaci ɗaya wani azabebben zufa ya wanke sa kana rawan da lips ɗinsa keyi ya tsananta karkarwa yayin da har hakoransa ke rawa har suna bugun juna saboda wani masifaffen abu da yaji yana yawo cikin kwanyar kansa, wani irin baƙon yanayi yaji ya taso masa da azaban ƙarfi, abinda bai taɓa jiba atsawon shekaru. Cike da dauriya da kuma fushi ya figi motar da gudu yayin da zuciyarsa ke wani irin azalzala idanunsa kuwa har yanzu dishi-dishi suke gani sanna, sai wani irin rawa jikinsa da lips inda keyi, cikin mintunan da basu gaza goma ba taji yayi Parking aƙofar gidansu. Cikin tsananin tsoro da ruɗu ta buɗe murfin motar, cikin sauri ta fice batare data lura da ɗan kwalinta da kuma hankief ɗin ta dake kan cinyar Moddibo ba. Da ƙarfi yafi gi motar cikin mintuna kaɗan ya isa gidan yana parking ya fito. Lokacin ɗaya ya jiƙe jikib saboda ruwan da ake cigaba dayi kamar da bakin ƙwarya. Cak ya tsaya Atsakiyar gidan nasu, ruwan na sauƙa atsakiyar kansa saboda masifeffiyar baƙon yanayi da yake ji ga kuma suya da raɗaɗin da zuciyarsa keyi, na firgicin saɓawa Ubangiji da yayi, tsoron Allah da tarin damuwa ne ya sanya idanunsa fara zubda wasu irin zafafan hawaye masu ƙuna. Rumtse idanun da yayi tare da furta. “Astagfirullah wa,atubu ilaik, Ya Allah kaine mafi sanin zuciyata, Yah Allah ka gafarta min ya Allah ka shafe min wannan zunubi, ya rabbi kada ka sake bani damar sake saɓa maka Yah Allah ka sani ban taɓa aikata makamancin hakaba,”. Gaba ɗaya muryarshi rawa takeyi, yayinda idanunsa ke kwaranyar da hawaye. Duk da ruwan na dukansa amma ko kaɗan baiga alamar zaiji sauƙin abinda ke damunsa ba. ji yayi tamkar ya ɗora hannunsa a ka ya rinƙa ihu da kururuwa. Duk da dauriyarsa kuwa, bai san sanda kuka ya kubce masa, domin duk sauƙan ruwan akansa ji yake kamar ana ƙara rurumashi wutar fitina a jikinsa, ga kuma ƙuncin zaciya da yake ji, Har lau haƙoran sake dukan juna suke nusa bada sautin Ƙat-ƙat-ƙat baki ɗaya jikinsa rawa yake tamkar mazari ahankali ya sunkuyar da kansa gani yayi yadda muhallin sa ya sake masifar nuna zalamarsa. Cikin mawuyacin hali ya dafe kansa da hannunsa na hagu murya narawa yace. “Wannan wace irin masiface? shin wannan wani irin abune mai wuyar jurewa me yake yafaru dani ne wai? Shegiyar yarinya mai fitintinun al'amura, ya Allah ka isarmin da cutar dani da tayi, Yah Allah kaga ita ta riskeni kaine shaida ni ban nufetaba, Allah ka isarmin kan wannan muguwar yarinya mai jikin zalumci Astagfurullah”. Ya ida maganar tare da fashewa da kuka, still dai yana tsaye acikin ruwan yana cigaba da dukansa, ganin sam kuma abin nasa yaƙi nitsuwa ne yasa ya nufi hanyar sashensa domin sakarwa da kansa ruwan ɗumi koda zaiji sauƙin abinda ke damunsa, abakin faradan Falon sa ya tsaya tare da zare rigar dake jikinsa kana ya zame wandon ya shanya ya rage daga shi sai boxer Kai tsaye toilet ɗin sa dake cikin Bedroom ɗinsa ya nufa yana shiga ya sakarwa da kansa ruwan ɗumi batare daya cire boxer ba yana tsaye ruwan ɗumin ya cigaba da zuba akansa amma babu abinda ke yawo a idanunsa kamar lokacin daya rungumi yarinyar ga wani masifaffen ƙamshinta da yake ji ajikinsa da ƙarfi ya matse jikinsa waje ɗaya kana cikin tsanananin tsoron Allah ya ci gaba istigfari. “Astagfurullah wa'atubu Ilaik ³ ya Allah na tuba kayafe min wannan abin da nayi. Ya Ubangijina na tuba”. Kai kawai yake girgiza wa cike da tashin hankali mara misaltuwa daya rufe idanunsa babu abinda yake hange face yanayin da suka kasance amota. Acan ɓangaren Khausar kuwa da gudu ta shiga gida tare da wucewa Falon su. Tsaye ta samu Mommyn ta cikin yanayin damuwa da tashin hankalin. Mommy na ganinta ta saki ajiyar zuciya mai nauyi tare da cewa. “Alhamdulillah Khausar kin dawo, gaba ɗaya hankalina ya tashi na kasa zaune na kasa tsaye, tunda Haiydar ya dawo ya faɗa min yanda ku kayi da Amina!”. Ida mgnar taba kallon yadda jikin Khausar ke ɗigar da ruwa ga wani rawa da jikinta keyi cikin jin ƙai da tausayawa tace. “Amina bata kyauta min ba. Wallahi Allah Amina bata taɓa yimin abinda ya ɓata min rai irin na yau ba, ya za'a yi cikin wannan hadarin cikin wannan yanayin ta baro min ke a makaranta. Yanzu waya dawo dake?”. Cikin karkarwa na tsoro da sanyi ga kuma zogin mari tace. “Uhhhmmm”. Ita kuwa Mommyn cikin sanyi tace. “Yanzun nan dama Abbanku nake jira? ya dawo dan baya nan na faɗa masa kina cikin makaranta. Yanzu yana dawowa ne akan zai ɗaukeni muje can ɗin”. Cikin sanyi da yanayin tsoro da kuma ruɗu Khausar ta dubi Mommy yayinda, jikinta ke rawa kamar zata faɗi. Kallonta Mommy tayi cike da tausayinta ta girgiza kai kana tace. “Gashi na sani Khausar yanda kike rikicewa idan kikaji rugugi kike fita hayyacinki idan kika ga walƙiya bare kuma kiji tsawa!. Gashi yau kuma ruwan yazo da wasu irin tswawwaki masu ban tsoro. Cikin rawan jiki ta sanya hannunta dake ta karkarwa ta janye Hijabinta kana ta kalli Mommyn Muryanta na rawa tace. “Yah Jameel ne ya kawo ni”. Ajiyar zuciya Mommy ta sauƙe kana tace. “Kai Ubangiji Allah yayi masa albarka. Allah ya saka masa da mafi kyawun sakamakon”. Kai Khausar ta gyaɗa still jikinta na tsuma tace. “Ameen Mommy bari in cire kayana”. Ta ida mgnar tare da wucewa Bedroom ɗin ta tana shiga ta kalli hannunta lokaci ɗaya ta sake shiga sabon tashin hankali, cike da damuwa ta yarfe hannunta kana tace. “Nashiga uku Ni Faɗimatuzzahara ina nasanya hannu na! Ni Batula?”. Duk da cewa tana cikin tsoro amma tana sane da inda ya zaro hannunta kai tsaye toilet ta Wuce tare da cire kayan jikinta ta sakarwa kanta ruwan ɗumi sabulu ta ɗauka ta mulke hannunta dashi kana ta shiga gogawa ajikin tiles dake jikin bangon tana Girgiza Kai kana tana mai Furta. “Innalillahi wa'inna ilahi rajiu'n Astagfirullah wa'atubu ilaik Subhanallah ya Salam Allah na tuba”. Da ƙyar ta iya yin wankan ta fito bayan ta ɗaura alawalan tare da buɗe Siff ta ɗauki dogon riga na roba baƙi ta sanya har zuwa lokacin jikinta na ƙamshin tularensa Sallaya ta shimfiɗa ta gabatar da Sallah kana ta riƙe carbi tana hawaye da Istigfari. Acan ɓangaren Moddibo kuwa bayan ya gama wanka al'wala ya ɗaura tare da fitowa har zuwa lokacin zuciyar sa na tsaye alamar zai samu nitsuwa Siff ya buɗe tare da ɗaukar Boxes ya sa sai kuma ya tsaya yana kallon kansa, ya tabbata idan yasa Jallabiya mutane zasu iya fahimtar halin da yake ciki wani dogon tsaki yaja. “Mitsssssssss!!! Yar iskar yarinya”. tare da sanya hannunsa ya matse muhallinsa da ƙarfi wai ko zai masa biyayya cikin yanayin tashin hankali ya kalli kuma sunkuyar da kansa tare da faɗin. “Wai wannan wacce iriyar Masifa ce!?”. Sake buɗe sabbin boxers ɗin sa dake cikin leda yayi ya ciro wani ƙarami wanda yake zaton zai masa kaɗan shiyasa ma bai taba sakasu ba, Cikin yamutsa fuska ya sanyashi, sosai ya matsesa sai dai har zuwa lokacin al'amarin azimunne. Wani boyel baƙi mai kyau ya ɗauka ya sanya kana ya feshe jikinsa da turarukansa cikin sanyin jiki ya fita zuwa Masallaci ya gabatar da sallah Azahar. A wunin wannan ranan dai baki ɗaya haka yayita agigice. Acan gidan Lamiɗo kuwa Hajiya Bunayya ce zaune akan 3sitter yayin da Amina ke gefenta riƙe da kofin shayi yana tururi. Anutse Hajiya Bunayya ta juya tare da kallon Amina data kai kofin shayin bakinta kana tace. “Amina yanzu ya kuke da Malam Jameel ne? nifa nagaji da wannan al'amarin kullum sai munga Abu kamar yaci sai kuma kiga abu ya sake ta ɓarɓarewa!”. Gyara zama Amina tayi tare da ajiye Cup ɗin tea kana tace. “Hmmm ba gwara ma muba akan Samira Sani, sufa duk abinda suke kamar anshuka dusa shi Moddibo na nan kamar Waliyyi baya fahimtar karatunta shu'umanci bare ya ratsasa kamar kurma baya ma sauraronta bare kuma ya sake mata fuska”. Ta gumi Hajiya Bunayya tayi tana cigaba da sauraren Amina. Amina ta cigaba da cewa. “Amma kinga gwara Ni dama Malam Jameel Yana da sauƙin kai sannan yanzu ya daina shash-shareni idan na gaishesa yana Amsawa cikin sakin fuska da mutunci mun koma kamar da duk da dai dama haka halinsa yake ga kowa”. Ajiyar zuciya ta sauƙe kana tace. “Kawai dai abinda nake gani Ummah kawai Abbah ya masa magana idan Abba ya masa magana kan cewa Ina son sa bazai ƙini ba, saboda yana da kirki yana da mutunci da kawaici ko ba komai kuma gidan dala yake domin nifa kuɗin mahaifinsa nafiso, badon kuɗin da suke da shiba, nafi son miji irin Modibbo mishkili, ba sake fuska dan sunfi iya soyayya”. Ajiyar zuciya Hajiya Bunayya ta sauke tare da gyara riƙon wayarta kana tace. “Anya Amina za'ayi hana kuwa? Ai gwara dai mujawo hankalinsa zaifi, kuma batun kuɗi yoh dama ai shi mukewa bauta domin duk abinda nake kashewa a wurin boka ina lissafawa kina shiga daga ciki zaku biyani”. Kwaɓe Fuska Amina tayi kana tace. “Kayya Ummah tun yaushe mukeyi amma abin baya wani kamasu gwara ma Malam Jameel Idan munyi munga Abu ya kama kwana biyu sai kuma ya dawo baya kula har kata! anata ƙara lissafin kuɗin da zan biya”. Kai Ummah ta gyaɗa kana tace. “Gaskiya dai kam in dai hakan zaiyi sai in faɗawa Mafaifinku yafi min kwanciyar hankali ma amma ko. Abbanku baza mu fuskance sa kai tsaye haka ba dole sai anja hankalinsa akan maganar”. Ta gumi Amina tayi tare da cewa. “Toh Ummah acanza wani boka mana?”. Saurin Kallonta Hajiya Bunayya tayi kana tace. “Wani boka muke dashi da yafi wannan?,Duk aikin sai yace ana wasa dashi sannan aikin kuɗi yake buƙata sosai kuma kinga Yanzu bani da kuɗi sosai Amina, kuma ai tunda muka canza boka Zurau wannan duk aikin da yake min yana ci”. Taɓe baki tayi tare da cewa. “Gaskiya Ummah asamu ayi aikin nan idan muka samu nashiga gidansu zamu fanshe duk kuɗin da muka kashe!”. Jinjina kai Ummah tayi kana tace. “Zanyi ƙoƙarin hakan in Allah ya yarda”. Acan ɓangaren su M Jameel kuwa bayan ya shiga gida ya sauya kayansa zuwa blue jeans da farin t-shirt mai dogon hannu kana ya gabatar da Sallah Azahar Yana idarwa ya nufi sashen Mahaifinsa zuwa lokacin ruwa ya tsaya bakinsa ɗauke da sallama ya shiga kana ya zauna kusa da Abbansa. Kallonsa Abba yayi bayan sun gaisa yayi gyaran murya tare da cewa. “Dama batun Company Adamawa ne acikin kayayyakin da aka kawo muga ya yanayin ingancinsu akwai atomfofi, Gyaleluwa da kuma sauran kayayyakin ya kamata kaje”. Jinjina kai M Jameel Yayi kana yace. “Toh shikenan Abba yaushe ne tafiyar”. Kallonsa Abbah yayi kana yace. “Insha Allah tafiyar zai kasance idan kun gama jarrabawar ɗaliban ku da zasu gama makarantar bana nasan zuwa lokacin hankalinka ya kwanta Asma'u da Bashir sun kammala Secondary School”. M Jameel kuwa jingina kansa da jikin kujeran yayi tare da lumshe idanunsa kana yace. “Hakane kam Alhamdulillah yanzu kam na gama sun gullarsu Asma'u”. Dai-dai lokacin da Hajiya Karima ta shigo falon Abba na cewa. “Kaga yanzu shikenan tun da kagama da wannan shungullan gaba ɗaya duk abinda ya shafi shungullana da kuma harƙoƙina, kasuwancina duk zan danƙasu ahannunka Babana. Domin ni girma ya fara zuwa Inason hutu”. Murmushi M Jameel Yayi kana yace. “Toh shikenan Abba babu damuwa duk abinda kace shi za ayi da izinin Ubangiji”. Murmushi Abba yayi har cikin ransa yake jin ƙaunar ɗan nasa saboda yanda yake masa biyayya ajiyar zuciya ya sauƙe kana yace. “Toh Nagode Allah yayi maka Albarka”. Duk abinda suka tattauna Hajiya Karima na rakuɓe tana jin tattaunawar su Amaryan Abban Jameel Hajia Turai ta shigo ganin Hajiya Karima atsaye yasa ta faɗin. “A'a Lafiya kike tsaye anan Hajiya Karima?”. Cikin sauri ta juya, sai asannan Abba da M Jameel suka juya suka ganta tsaye. Murmushin da bai wuce saman laɓɓabanta ba tayi kana tace. “Yanzu na iso ina gyara labule nai”. Ita dai Hajiya Turai batace komai ba ta ƙarasa shiga falon kana Hajiya Karima tabi yo bayan suka cigaba da hira. Washe gari. Cikin sanyin jiki da damuwa Khausar ta shirya cikin Uniform ɗin ta dake haska fatarta baki daya ta kasa sakewa da zaran ta tuna inda ta sanya hannunta sai taji tashiga matsanancin tashin hankali. Cikin sanyin jiki ta fita tare da nufar inda motarsu ke fake Amina ce tafito hannunta riƙe da lunchbox ɗin Aminu dai-dai lokacin da Lamiɗo ya fito daga sashen Gimbiya Dadu da fuska a tsuke ya kalli Amina tare da cewa. “Banaso Amina kada ki sake yi min abinda kikayi jiya banaso haka ki kiyayeni! Ki kiyayeni!”. Ƙasa tayi da kanta kana tace. “Toh Abba kayi haƙuri”. Sannan ta juya ta shiga, kana su Khausar ma suka shiga mota ko acikin mota Khausar jingina bayanta da jikin kujera tayi tare da damƙe hannunta ahaka har suka isa makarantar. Anutse ta fito ta tashiga hall da suke Exam kai tsaye bencin da number ta ke kai ta nufa tare da zama kana ta dafe kanta ba jimawa Malam Isa ya shigo ya fara raba musu Booklet da questions na Economics. Kallon Khausar data dafe kanta da hannu biyu yayi kana yace. “Lelewal meke damunki?". Da sauri ta ɗago kanta ta kallesa sai kuma ta girgiza kanta cikin sanyin murya tace. “Ba komai Malam”. Question peper ya ajiye mata kana ya cigaba da rabawa sauran. Cikin mutuwar jiki Khausar ta riƙa yin amsarin Questions ɗin tun kafin a miƙa wa wasu Questions pepar tuni ta gama Amsawa kwantar da kanta akan deks ɗin tayi tana godewa Allah daya sa basu da Exam din Moddibo da batasan da idon da zata iya kallon sa ba. Moddibo kuwa tunda yashigo makarantar ya wuce office ɗin su ya zauna cikin zullumi da damuwa. Ahankali M Jameel ya fito daga class da yake teaching hannunsa riƙe da booklet ya nufi Office ɗinsu bakinsa ɗauke da Sallama yashiga zaune ya samu Moddibo idanunsa na rufe kana lips ɗin sa na rawan sanyi ahankali. Booklet ɗin ya ajiye tare da zama gefensa kana yace. “A.J meke damunka?”. A hankali Moddibon Ya jujjuya idanunsa dake lunshe yayi kana ya Girgiza masa kai tare da cewa. “Bakomai”. Kallonsa M Jameel Yayi kana yace. “Ya zaka ce min bakomai A.J ke faɗa min meke damunka ko dai baka da lafiya ne?”. Ajiyar zuciya ya sauƙe tare da gyaɗa masa kai. Cikin damuwa M Jameel yace. “Toh meke damunka?,Ka faɗa min abinda ke damunka mana”. Sai asannan Moddibo ya buɗe Idanunsa cikin raunin murya tamkar mai shirin fashewa da kuka yace. “I don't know J I really don't know what's wrong with me WLH BAN SANIBA, BANSAN MEKE DAMUNA BA J”. Da Mamaki M Jameel ya kallesa kana yace. “How A.J kamar ya bakasan meke da munka ba”. Langwaɓar da kai Moddibo yayi cikin yanayin damuwa da tashin hankali ya kalli M Jameel daya tsaresa da ido ya sauƙe Idanunsa ƙasa kana yace. “Bansani ba J bansan meke damuna ba Na dai san bana jina dai-dai ina cikin ɗimuwa”. Ya ida maganar yana mai lumshe idanunsa sam ya rasa taya zai fara faɗawa M Jameel yanayin da yake ji ajikinsa. Ajiyar zuciya M Jameel ya sauƙe kana yace. “To ko dai zazzaɓi ne?”. Girgiza kai Moddibo yayi still cikin raunin murya yace. “A'a”. Ahankali M Jameel ya sake cewa. “Toh ko Kanka ke ciwo?”. Still Kai Moddibo ya sake Girgiza masa alamar a'a. Numfashi M Jameel ya fesar kana yace. “Toh ko dai cikin kane?”. Nan ma kai Moddibo ya Girgiza kamar zai fashe da kuka. Tagumin M Jameel Yayi kana yace. “Toh meke damunka?”. Lumshe idanu Moddibo yayi cikin sanyin murya mai rauni ya buɗe idanunsa tare da kallon M Jameel daya tsaresa da Ido kana yace. “J bana jina dai-dai ina jin kamar akwai wani abu da nake buƙata amma bansan menene ba”. Murmushi M Jameel yayi kana yace. “Toh me kake buƙata?”. Girgiza kai Moddibo yayi tare da buɗe hannunsa kana cikin sanyin murya yace. “Idont know J nima ban sani ba bansan me nake so ba amma inaji kamar akwai wani abu da ɗan Adam yake buƙata acikin rayuwarsa wanda nima nake buƙatarsa kusa sani, daga jiya zuwa yau amma bansan menene bane”. Kallonsa M Jameel Yayi tare da kallon yanda idanunsa suka sauya launi zuwa Ja tun safe da suka zo ya lura da hakan tamkar mai mayen bacci kana ya lura da yanda lips ɗin sa ke rawa sannan ya lura da yanda bini-bini yake matse ƙafafunsa. M Jameel na cikin Kallonsa. Moddibo yayi miƙa tare da matse ƙafafunsa kana lips ɗin sa suka shiga rawa sai kuma ya runtse Idanunsa. Murmushi M Jameel yayi kana yace. “J kodai kana jin kana ɓuƙatar mace akusa da kai ne?”. Lokaci ɗaya Moddibo yaji zuciyarsa ya tsinke da masifar ƙarfi ajiyar zuciya ya saki tare da kallon M Jameel ji yake tamkar ya fashe da kuka ko zaiji sauƙin abinda ke damunsa sunkuyar da kai ƙasa yayi cikin wata raunan'niyar murya mai sanyi yace. “Ban sani ba J”. M Jameel yace. “Toh mutafi gida mana tunda na gama abinda nake kai kuma naga kamar baka da komai”. Kai Moddibo ya gyaɗa kana ya miƙe tare da yin miƙa da ayau ya zame masa jiki domin baya minti goma mai kyau sai yayi miƙa. Kallonsa M Jameel yayi dan yanda yaga Modibbonsa ya tashi ta saman rigar duk da kuwa boxes biyu ya saka duk dan ya suturta jikinsa ɗagowa M Jameel yayi tare da kallon fuskarsa yayi Murmushi. Fita Moddibo yayi M Jameel yabi bayansa dai-dai lokacin da aka kira sallar Azahar acikin masallacin dake makarantar. bayan sun Idar suka fito suka shiga mota M Jameel ke driving yayin da Moddibo ke gefen mai zaman banza idanunsa alumshe duk abin duniya ya Ishesa. Suna isa gida M Jameel yayi Parking ya fita kai tsaye sashen Innayi ya wuce ya karɓa musu abinci Moddibo kuwa cikin mutuwar jiki ya wuce sashen sa ya kwanta. Ba jimawa M Jameel ya dawo hannunsa riƙe da Warmers da kuma Plate kwance ya samu Moddibo akan 3sitter yayi rub da ciki idanunsa akan ƙofar falon. Ƙarasa shiga falon M Jameel Yayi tare da zama aƙasa kana ya kalli Moddibo da faɗin. “Saƙƙo muci abinci idan muka gama sai muje kaga Dr”. Girgiza kai Moddibo yayi cikin sanyayyar Murya yace. “Bana jin yunwa bana son cin komai”. Buɗe Warmer M Jameel Yayi tare da cewa. “Toh Meyesa haka J?”. Cike da raunin murya tamkar wanda ke shirin fashewa da kuka yace. “Ban saniba nima”. Dariya mara sauti M Jameel Yayi kana yace. “A.J Na fahimceka fa kamar *Mace* kake buƙata acikin rayuwarka!”. Cikin sauri Moddibo ya lumshe idanunsa jin suna tsats-tsafo wa da hawaye, miƙewa yayi tare da wucewa Bedroom ɗin sa yana shiga yasa key ya rufe. M Jameel kuwa jingina bayansa da jikin kujera yayi tare da fashewa da dariya harda riƙe ciki. Moddibo kuwa yana kulle ƙofar ya juya ya kwanta ruf da ciki tare da lumshe idanunsa yayin da ƙwaƙwalwar sa ta shiga tariyo masa moment da suka kasance acikin mota lokaci ɗaya Muhalinsa ya shiga harbawa da ƙarfi tamkar zai fisge ya fito, yayin da lips ɗin sa suka shiga rawa har haƙoransa na haɗuwa kar-kar-kar. Batare daya shirya ba yaji hawaye suna bin kuncinsa shi kansa baisan meyake so ba bai san meke faruwa dashi ba yakasa sanin yana yin da yake ciki ji yayi kawai yana kuka hawaye na bin kuncinsa yana sheshsheƙa. Miƙewa yayi cikin rashin sanin madafa shin ya zaiyi da wannan jarabar tun jiya yake fama da zaran ya rufe Idanunsa yanayin da suka kasance da yarinyar ne yake gani. M Jameel kuwa dambun shin kafa dayaji vegetables da soyayyen naman kaza dake tashin ƙamahi ya zuba a Plate ya fara ci yana cikin ci ne wayarsa dake gefensa ya hau ruri. Ahankali ya sanya hannunsa ya ɗauka Turkey Kawai ya gani babu Number. Picking yayi tare da kaiwa kunnensa yana dariya yace. “Yaushe kaje Turkey?”. Murmushi Jalaludeen yayi kana yace. “Na kusa kwana biyar acan ai”. Kai M Jameel ya gyaɗa kana yace. “Lallai dai kam yayi kyau ya gida”. Gyaran murya Jalaludeen yayi tare da cewa. “Lafiya wai meyasamu Aliyu ne”. M Jameel na ajiye cokalin hannunsa yace. “Nima kaina ban sani ba”. Dariya Jalaludeen yayi kana yace. “Mace ta fara shiga rayuwarsa kenan. Aure fa yake da buƙata yana da ƙaƙƙarfan sha'awar da tuntuni na kwantar masa da shi”. Zare Ido M Jameel Yayi kana yace. “Auuu Jalaludeen kenan kaine ka maida mu waliyan dole?”. Cikin sauri Jalaludeen yace. “A'a Ni ban mayar daku mata ba, amma dai kawai nasan Aliyu nada ƙarfin sha'awa na masifa idan har aka bar shi da wannan sha'awar zai iya zame masa masifa kana zai iya jefashi acikin damuwa gashi naga burinsa a lokacin yayi ilimi mai zurfi, kuma in ka tuna a lokacin yana yawan fama da ciwon ciki”. Dafe kunci M Jameel Yayi yana saurarensa. Murmushi Jalaludeen Yayi kana ya cigaba da cewa. “Tun haɗuwar mu na farko kafin ku fahimci wanene ni kafin ku fahimci komai akaina, kana tun kafin afahimci wanene ni asan komai akaina na bashi abinda yasha wanda ya karyar masa da ƙarfin sha'awarsa har yake ji kamar baya buƙatar mace acikin rayuwarsa”. M Jameel ya gyara zamansa tare da cewa. “Ikon Allah”. Jalaludeen kuwa cikin yanayin su na can yaci gaba da cewa. “Toh ajiya akwai abinda yafaru ko dai mace tashiga rayuwarsa ko dai akwai macen data kama jikinsa wannan dalili yasa gaba ɗaya takarya alƙadarin abinda ke jikinsa!”. Ajiyar zuciya M Jameel ya saki kana yace. “Toh fa”. Murmushi Jalaludeen yayi tare da faɗin. “Kai kuma kwaɗayin ka ne ya kaika dana bashi maganin yana cikin sha kawai ka amshi kofin kasha shiyasa kuka kasance atare haka amman ai kai naka ba kamar nashi bane ”. Murmushi M Jameel Yayi kana yace. “Amma dai gaskiya Jalaludeen baka da mutunci”. Dariya Jalaludeen yayi kana yace. “Nifa bance komai ba gaba ɗaya abinku lafiya lau yake kawai dai sha'awar ce na kwantar”. Girgiza kai M Jameel Yayi kana yace. “Toh yanzu shi kuma wannan ya za'ayi dashi dan yanzu wallahi ya tashi ya tafi ɗaki kamar zaiyi kuka”. Murmushi Jalaludeen yayi kana yace. “Kukan ma yakeyi yanzu”. Ware ido M Jameel Yayi kana yace. “Lallai dai kam maza sun gamu da aiki kenan”. Jinjina kai Jalaludeen yayi tare da cewa. “Gaskiya yanayin daya ke ciki ne awahale yake haka ya wuni jiya still haka ya kwana gashi kuma yau ma ya wuni haka”. Cike da tausayawa M Jameel yace. “Toh yanzu ya za'ayi ?”. Girgiza kai Jalaludeen yayi tare da cewa. “Gaskiya ban sani ba dan bani da yanda zan mishi kawai abune daya zo masa babu yanda za'ayi haka zaita rayuwa mafita ɗaya ne kawai yayi ƙoƙari yayi aure”. Ajiyar zuciya M Jameel ya sauƙe tare da cewa. “Ok zamu yi ƙoƙari muga mai ya dace tunda gashi dama duk abinda ya dace mun gama”. Jinjina kai Jalaludeen yayi kana yace. “Masha Allah amma yanzu ka samu ruwan ɗumi kasa masa laimun tsami yaji kana ka sanya zuma yaji sai ka bashi yasha zai ɗan ji sauƙi”. Kai M Jameel ya gyaɗa kana yace. “Toh shikenan ba matsala mun gode”. Sallama sukayi tare da katse kira. Miƙewa M Jameel Yayi yashiga cikin kichen dake falon ya buɗe Flaks dake ɗauke da ruwan tea ya zuba a Cup lemun tsami ya duba yaga babu rufe Cup ɗin yayi ya nufi cikin gadin ɗin gidan ya tsunko guda biyar sannan ya dawo ya wanke tare da matse su duka acikin shayin kana ya buɗe kofin roban zuma yasa. Fita yayi a kichen ɗin ya nufi Bedroom din Moddibo yayi Knowking ƙofar. Dai-dai lokacin da Moddibo ya cire kayan jikinsa ka ya zura Jallabiya kasancewar boxers ya takure masa jiki har yana jin mallakinsa na yimasa ciwo saboda yanda ya takuresa ya hanasa miƙewa cikin gajiyawa ya mike ya cire boxes ɗin tare da cewa. “Bari naga iya inda zaka tsaya uban ƴan zalamammu”. Yayi maganar yana kallon jikin nasa daya miƙe ya tsaya acikin Jallabiyar. Muryar M Jameel yaji yana cewa. “A.J ka buɗe min ƙofar mana in baka magani”. Daga ciki Moddibo ya buɗe masa ƙofar. Kallonsa M Jameel Yayi sai kuma ya kalli yanda ya ɗaga rigar kawar da kai gefe yayi yana jin dariya na neman kufce masa. Kofin dake riƙe ahannunsu ya miƙa masa. Cikin Sanyayyar muryarsa yace. “J Me wannan?”. M Jameel ya Kalli kofin kana yace. “Kasha mana zaka ji sauƙin abinda ke damunka na fahimci meke damunka A.J”. Moddibo bai sake cewa komai ba ya amshi Cup ɗin ya koma bakin gado ya zauna tare da kafa kansa ya shanye tass kana ya ajiye kofin, cikin ikon Allah lokaci ɗaya yaji zufa ya fara sauƙa masa Atake yafara jin abinda ke damunsa na sauƙa kaɗan-kaɗan amma still jikinai ɗin na nan amiƙe ahankali yaji lips ɗin sa ya daina rawan zamewa yayi ya kwanta akan gadon yana sakin ajiyar zuciya akai-akai. Acan gidansu Khausar kuwa zaune suke afalon Mommy suna cikin hira ka jiyo sallama. Cikin sauri Haiydar ya ɗago kansa tare da cewa. “Laaaaah....! *Littafin SAKAYYAH na kuɗine biya ki karanta cikin Aminci da salama babu haƙƙin kowa a kanki yar uwa 1k ne kacal 0661110170 GTBank AISHA ALIYU GARKUWA. Sai ki turo min shaidar biyanki ta WHATSAPP 09097853276, sai in saki a Group na ɗin da zanke posting. Ko kinga littafin SAKAYYAH a waje na satane* *By* *GARKUWAR MARUBUTA* [24/07, 6:14 AM] Halimatu A/rahman Sadeeya: Spjnyh. Miƙewa Haiydar yayi kana ya nufi ƙofar falon fuskarsa ɗauke da murmushi yace. “Oyoyo Uncle Naseer”. Khausar dake zaune kan 1sitter sanye cikin riga da baƙin wando Pencil da riga pinch color mai gajeren hannu gaban rigar an rubuta Never Give Up manyan boobs ɗin ta sun cika gaban rigar yayin da bajejjen ƙugunta ya baje acikin wandon, kanta sanye da hular Net baƙi gashinta ya zubo ta gefen wuya, a hankali ta juyo ta kallesa tare da faɗaɗa fara'ar dake saman fuskarta kana tace. “Laaa Uncle Naseer”. Shi kuwa Naseer ido ya zuba mata yana sakar mata da wani irin shu'umin murmushi yayin da yashiga bin ilahirin jikinta da kallo wani irin kallon Up and Down yake mata yana jin komai nata na kars burgesa soyayyar ta na kuma ninkuwa a ransa. Cikin wani irin salo kana still Idanunsa na kanta ya wani lumshe ido afili ya furta. “Masha Allah Matata ta girma”. Mommy dake zaune kan 3sitter tayi murmushi tare da cewa. “Masha Allah Naseer mutanen India kwanan nan mukayi magana da Aunty Jameela kece min ka kusa dawowa Ashe-ashe dawowa yazo ma”. Murmushi yayi kana cikin yanayin zumuɗinsa yace. “Aidai kam suma Surprised ɗin su nayi babu wanda yasan dawowana akwanan nan kawai sai ganina sukayi”. Cike da kulawa Mommy tace. “Masha Allah sannu da zuwa ka iso”. Raudat da Ramadan dake zaune suka mike tare da zuwa suka riƙe hannunsa,hannun Raudat ya riƙe tare da ɗagata sama kana yace. “Iyeee Baby Raudat Masha Allah an girma anyi kyau. Amma dai duk da haka Matas tayi miki wayau ta fiki kyau”. Murmushi Mommy dake zaune tayi kana tace. “Haka dai kace”. Ware ido yayi kana idanunsa akan Khausar yace. “Allah kuwa Mommy dubi fa Khausi na tafita kyau”. Khausar kuwa lallausan tafin hannunta tasa ta rufe fuskarta. Sai kuma ta miƙe ta nufi kichen ta ɗauko drinks da Snacks sai kayan Friut tafi to masa dashi. Har zuwa lokacin batayi magana ba sai dai da zaran sun haɗa ido zata sakar masa da ɗan guntun murmushi kamar yanda shima yake sakar mata. Haiydar kuwa da sauri ya saki hannun Naseer kana ya nufi sashen Hajiya Bunayya yana faɗin. “Ummah,Ummah ga Uncle Naseer kizo ku gaisa". Miƙewa Ummah tayi fuskarta ɗauke da murmushi Amina ma miƙewa tayi tana murmushi tabiyo bayansu. Cike da farin ciki Amina tace. “Uncle Naseer mutanen India”. Washe baki Naseer yayi domin shi mutum ne mai fara'a da son nuna shi wani ne, kana ga fafa da iyayi baya ga haka yana da budeɗɗen ido da son holewa. Ita kuwa Hajiya Bunayya kallonsa takeyi da murmushi afuskarta tace. “Naseer sai ganinka mukayi babu sanarwar anyi karatu angama ka dawo Nigeria kenan?”. Sha fa sumar kansa yayi yana shan Fruit da Khausar ta kawo masa yace. “Wallahi kuwa Ummah nazo ganin Matata ce muyi aure in ɗauke ta mutafi. Amma Ziyara nazo yi muku zan koma da matata, dan bazan iya zaman Nigeria ba”. Murmushi Mommy tayi kana tace. “Ayyah Naseer ai nan ma muna da waja-je masu kyau kodai India sunfi mu Weather mai kyau ne?”. Girgiza Kai yayi tare da cewa. “No Mommy bawai Weather mai daɗi ba kawai dai can ɗin zan samu aiki ne sannan gaskiya ni yanzu bazan iya rayuwar Nigeria ba”. Ya ida maganar yana ya mutse fuska cike da Iyayi. Murmushin da bai wuce saman laɓɓaba Hajiya Bunayya tayi kana tace. “Aikam dai kam yayi kyau Allah ya taimaka bari na koma ina aiki”. Ta ida maganar tare da miƙewa dan Allah ya sani ya ƙona mata rai da batun ya aure Khausar su koma India. Amina kuwa siririn tsaki taja cike da jin haushin yanda Naseer ke Shish-shigewa Khausar ta miƙe tabi bayan Hajiya Bunayya suka fice. Bayan fitarsu Mommy ta miƙe tashiga Kichen Haiydar ma miƙewa yayi tare da ɗaukar Ramadan da Raudat suka fita danmai yi musu lesson yazo. Falon ya rage daga Khausar sai Naseer, Ahankali Khausar ta miƙe da niyyan barin falon cikin sauri Naseer yace. “Ohh My dear Wife Why are you going?”. Murmushi Khausar tayi aranta tace Ohh Uncle Naseer sam bazai canza ba, wannan kalma ya riƙe ta tun yarinta alokacin batasan ma'anarsa ba amma yanzu da zaran ya faɗa kunya take ji wai matarsa ko kunya faɗa agaban su Mommy baya ji. Anutse ta dawo ta zauna a inda ta tashi, cikin tsareta da Ido yace. “Tunda baki gaisheni ba bari in gaishe ki”. Cikin sauri tayi ƙasa da kanta kana tace. “A'a Uncle Naseer ina yini ya karatu fatan ka dawo Lafiya?”. Sumar kansa ya shafa kana yace. “Karatu Alhamdulillah ya naki karatun??”. Murmushi Khausar tayi kana tace. “Alhamdulillah Uncle Naseer nan da kwana goma zamu gama Secondary school Insha Allah”. Washe baki yayi yana binta da wani irin kallon yace. “A'a Masha Allah Abu yayi kyau kenan abu zai tafi dai-dai yanda aka tsara”. Murmushi tayi tare da sunkuyar da kanta ƙasa tana wasa da yatsun hannunta. Ɗago kansa yayi tare da miƙewa ya koma kusa da ita. Cikin wata narkakkiyar murya ya kalleta tare da cewa. “Khausar ina fatan baki manta da maganar mu bako?”. Murmushi tayi still ba tace komai ba sai ƙasa da tayi da kanta tana cigaba da wasa da yatsun hannunta”. Shi kuwa Naseer sake narkar da muryarsa yayi tare da faɗin. “My Khausi kinsan dai ina sonki, ke tawa ce inaji Ajikina Ubangiji ya halicce ki ne domin ni kaɗai kinsan ina matuƙar ƙaunarki ina burin ki kasance matata ke ta dabance ina miki sahihiyar ƙauna bani da burin daya wuce mu zamto ma'aurata in mori ni'imar da Allah ya halitta miki”. Batare data ɗago kanta ba tace. “Uhm”. Shi kuwa wani narkar da fuska yayi tare da lanƙwasar da harshe kana yace. “Meyesa ne komai nace sai kice Uhm?. Yanzu ke kanki bakya jin kina so kiyi Aure ne? aike kanki kin girma kin kai matakin da akan kanki zaki buƙaci na miji atare dake musamman ma na miji irina wanda zai iya gamsar dake tare da biya Miki duk kan buƙatunki ko ba haka bane?”. Lokaci ɗaya Khausar ta kwaɓe fuska cikin yanayin rashin jin daɗi da kuma rashin tsammanin abinda ya faɗa ta ɗago kanta tare da Kallonsa sai kuma ta kawar da kanta gefe fuska a tsuke. Shiko sake narkar da murya yayi tare da tsira mata Idanu kana yace. “Shifa rayuwar nan baya tafiya dai-dai dole sai ansamu dai-dai-to atsakanin halittar Namiji da mace, rayuwar nan bata da wani daɗi idan har babu mace akusa da namiji, haka itama mace rayuwar bata mata daɗi idan har babu Namiji akusa da ita, musamman idan anfara tafiya irin matakin shekarun kin nan daga Sha tara, Ashirin, Ashirin da ɗaya,Asirin da biyar, Talatin,har zuwa talatin da biyar dole tana buƙatar Namiji”. Ya sake narkar da murya yana binta da wani shu'umin kallo yace. “Muyi Aurenmu Khausar zaki ci gaba da karatunki a India sai kije kiyi karatunki acan”. Ƙasa ta sake yi da kanta kana cikin yanayin ɓacin rai ta ɗago batare data yarda sun haɗa ido ba tace. “Ni bana sha'awar zuwa India nafiso in zauna an ƙasata kusa da Mommy na bana buƙatar duk wani abu da zai nesanta ni da ita da kuma ƙasata domin duk abinda India take dashi ai muma muna da shi harma fiye da nasun”. Cikin sauri ya sake Matsawa kusa da ita tare da sanya hannunsa zai kamata. Da mugun sauri ta kauce ranta babu daɗi ta kallesa kana tace. “Ya haka Uncle Naseer mai yasa zaka kama min hannu?”. Ido ya lumshe yana jin sautin muryarta na ratsa shi sai kuma ya buɗesu akanta tare da cewa. “Ohh My God wai Khausar har yanzu baki waye bane? me haka kamar ba ƴar zamani ba!? Dan na taɓa ki ai bawani abu bane kada ki manta tun kina ƙarama ko su Abba sun sani ke mallaki nace idan Ubangiji ya nufa”. Fuska ta sake ɗaurewa kana cikin sauri tace. “Toh kabari sai Ubangijin ya nufa kasamu. Shaidu sai inzama mallakin naka”. Ta ida magarta tare da miƙewa tabar wajen. Binta yayi da kallo bajejjen ƙugunta wanda duk takun da tayi sai sun motsa tamkar da gangan take juyasu. Dai-dai lokacin kuma Mommy ta fito daga kichen yana ganin ta ya miƙe tare da cewa. “Mommy bari in isa wajen Yafendo Dadu”. Shi ɗin ɗan ƙanwar Gimbiya Dadu ce, Ya ida maganar tare da ficewa kai tsaye sashen Gimbiya Dadu ya nufa bakinsa ɗauke da Sallama ya shiga falon. Gimbiya Dadu dake zaune tana shan Fruit ta Washe baki kana tace. “Nasiru lallai mutanen India masha Allah sannu da zuwa”. Zama yayi daga gefenta yana murmushi kana yace. “Yafendo fatan mun sameku lafiya?”. Cike da farin ciki tace. “Lafiya lau Nasiru ina ƴar Uwata ƴar Autanmu”. Zamansa ya gyara tare da cewa. “Tana lafiya tace in gaisheki”. Kai ta gyaɗa kana tace. “Ayyah Ina Amsawa”. Gyaran murya yayi tare da fuskantar Gimbiya Dadu kana yace. “Yafendo na gama karatuna yanzu na dawo sannan na dawo da burin yin Aure. Ya maganar mu da khausar tana nan dai ko?”. Ajiyar zuciya mai nauyi Gimbiya Dadu ta sauke tare da lumshe Idanunta kana ta saki wani shu'umin murmushi tare da kallonsa kana tace. “Sosai ma kuwa maganar ku tana nan mai zai hanata da izinin Ubangiji maganar ku tana nan baka da matar data wuce Khausar yau ɗin nan zan yiwa Abbansu maganar”. Cike da farin ciki ya saki sanyayyar ajiyar zuciya kana yace. “Kai Alhamdulillah Yafendo na naji daɗi”. Murmushi kawai tayi shi kuwa miƙewa yayi bayan sun sake taɓa hira ya tafi. Bayan kwana uku. Ahankali Khausar ta sauƙa daga motar dake kaisu makaranta hannun riƙe da Raudat ta nufi ajinsu ta kaita kana ta dawo tashiga ajinsu Lokacin har an fara raba booklet kallonta Malam Isma'il dake raba Booklet ɗin yayi kana yace. “Lelewal mai yasa kike son zuwa letti ne Exam ɗin ma baza ki fito da wuri ba?”. Langwaɓar da kai Khausar tayi tare da cewa. “Ayyah Malam ayimin afuwa”. Harara Samira Sani dake bayan ta ta watsa mata cike da tsanar ta Asma'u dake gefen ta ta girgiza kai domin ita dai ta rasa me. Khausar ta tsare musu suka tsaneta. Khausar kuwa zama tayi Malam Isma'il ya bata Booklet da kuma Quatons peper Na Arabic da zasuyi yau ma kamar kullum tun kafin a gama rabawa Khausar tashiga answering Questions ɗin cikin mintunan da baza su gaza ashirin ba ta kammala. Acan office ɗin Moddibo kuwa zaune yake ya jingina bayansa da jikin kujera yayin da ya ɗaura ƙafarsa ɗaya kan ɗaya akan deks ɗin Idanunsa na lumshe. Cikin sauri ya buɗe Idanunsa tare da jan dogon tsaki. Domin da zaran ya rufe idanunsa babu abinda yake gani sai moment da suka kasance da yarinyar cike da damuwa ya sauƙe numfashi kana aƙasan ransa yace. “Na godewa Allah da yasa karatun yaran nan yazo ƙarshe kana naji daɗi da cewa sun gama Exam ɗina, bazan sake shiga ajinsu ba”. Da sauri ya runtse Idanunsa haka nan yake jin kunyar kansa da kansa ya rasa ta yanda zai fassara al'amarin yasan tun farko yarinyar bata da kunya bare kuma wannan abu ya faru shin taya zai iya haɗa ido da ita?. Anan sashin su kuwa. Atare Khausar da Asma'u suka fito daga Area class ɗinsu har zasu wuce suka hango M Jameel tsaye. Abakin Office ɗin su Moddibo. M Jameel ne tsaye ya jingina bayansa da jikin ƙofar yayin da Amina ke tsaye gefensa cikin iyayi da yauƙi ta kashe murya tare da cewa. “Malam sai gobe idan Allah ya kaimu zan dawo ko Principal ya dawo na amshi result ɗina”. Anutse M Jameel ya juya ya kalleta tare da cewa. “Ok Allah ya kaimu ki gaida gida”. Sake karya murya tayi cikin tsaresa da ido tace. “Toh gida zaiji Malam kaima ka gaida gida”. Jinjina kai yayi batare daya sake kallonta ba yace. “Gida zaiji”,Juyawa tayi tabar wajen. Dai-dai lokacin da Asma'u da Khausar suka iso a tare Kallonsa Khausar tayi tare da cewa. “Barka da rana Yah Jameel”. Murmushi ya sakar mata kana yace. “Yawwa Khausi bar ka dai yanzu kam an zama manyan ƴan mata ankusa agama Secondary school a huta a shiga babin girma ko?”. Jinjina kai tayi cikin jin daɗi ta kalli Asma'u kana tace “Ai lallai dai kam bari kawai Yah Jameel jinmu nake tamkar ansaki tsuntsuwa daga sheƙarta. Wani irin daɗi mukeji mun kusa mu rabu da rayuwar bauta rayuwar duka cin zali, kaɗe ɗan kwali, harara, tsawa, hantara,”. Kallon ta M Jameel Yayi tare da juya idanunsa zuwa office ɗin ya mata alamar Moddibo na ciki. Cikin sauri ta sanya hannunta ta rufe bakinta tare da barin wajen bayanta Asma'u tabi tana ƙyalƙyala dariya tare da cewa. “Khausar ga Moddibo na miki magana wai kije”. Dariya M Jameel yayi ganin Cikin sassarfa Khausar ta fice daga wajen batare data yadda ta juya ba. Moddibo kuwa na zaune a office duk Maganar da sukayi akunnensa da zaran sautin muryanta ya ratsa kunnensa zaiji tsikar jikinsa ya tashi tamkar ana stikaresa da allura hakan yasa ya runtse Idanunsa da ƙarfi kana yayi shiru. Allah ne kaɗai yasan yana yin da yake ciki. Khausar kuwa na fita wajen motarsu ta nufa ta samu duk su Amina su shiga ita kadai ake jira tana zama Driver yaja suka tafi. Asma'u kuwa na fita ita da Bashir mai Napep ɗin su ya iso ya ɗauke su suka tafi. Washe gari da yamma bayan Khausar sun dawo makaranta misalin ƙarfe Uku ta fito cikin wata Bugaggiyar shadda milk color anyi masa ɗinkin dogon riga da kuma zubi da akayi sa da Coffee zare fuskarta ɗauke da light Make-up yayin da tayi ɗaurin Aysha Buhari ta zuba jelar gashinta ta gefen dama dake fitar da sanyayyan ƙamshi kana ta yafa milk colour gyale akafaɗarta Hannunta riƙe da jaka Coffee haka ma takalmin Half cover coffee color jikinta na fitar da sanyayyan ƙamshin tularen Balila da kuma Sedection. Kai tsaye Bedroom din Mommy ta nufa bakinta ɗauke da sallama tashiga ganin Mommy Bata ciki yasa ta fito tare da nufar kichen. Tsaye ta samu Mommy tana yanka albasa. Mommy na ganinta tace. “Har kin gama shiryawa?” Kai ta gyaɗa kana tace. “Eh Mommy na gama shiryawa”. Jinjina kai Mommy tayi tana cigaba da yanka albarsar tace. “Idan kinje ki Gaishe da Ummin Asma'u”. Kai ta gyaɗa tare da gyara rikon Handbag din ta kana tace. “Insha Allah zata ji Mommy”. Dai-dai nan suka jiyo Sallamar Naseer afalo, cikin sauri ta kalli Mommy sai kuma ta ɓata fuska lokaci ɗaya ta nemi fara'ar dake fuskanta ta rasa. Kallon mamaki Mommy tayi mata kana tace. “Ya dai haka daga jin muryan sa kin wani tsuke fuska sai kace wanda yazo miki da wani mugun abu”. Girgiza kai tayi tare da cewa. “Babu komai Mommy”. Girgiza kai Mommy tayi tare da fita tana cewa. “A'a wa nakeji kamar Naseer mutan India”. Yana zaune kan kujera ya gyaɗa kai tare da cewa. “Eh Mommy nine”. Dai-dai lokacin da Khausar ta fito miƙewa yayi idanunsa akanta yace. “Wooow Masha Allah”. Sam ya mance da Mommy dake tsaye a wurin. Gaba ɗaya imaninsa ya tafi gareta cike da zalama ya nufi Khausar tamkar zai rungumeta yana faɗin. “Wowww my dear Wife you look so georoures, Fantastic, beautiful you look so Pretty”. Khausar kuwa ganin yanda yake matsota zai Rungumeta yasa taja baya da sauri tare da cewa. “Nagode. Mommy kuwa kallon ikon Allah take ganin yanda baki ɗaya hankalinsa ya tafi kan Khausar da alama ya mance da tana wajen. Gyaran murya tayi tare da cewa. “A'a Naseer ka zauna mana akawo maka abin taɓawa mana”. Girgiza kai yayi da faɗin. “A'a Mommy Nagode”. Itako Khausar ɓata fuska tayi babu walwala atare da ita tace. “Mommy na tafi". Cikin sauri ya mike tare da bin bayanta kana yace. “My dear Wife Ina Zakije?”. Ataƙaice tace. “Unguwa”, Cikin yanayin zumuɗinsa yace. “Bari in sauƙe ki”. Mommy kuwa ita kanta rawan kansa ya bata tsoro ganin yanda yake nuna zalamarsa afili kamar kura yaga ɗanyen Nama!”. Da sauri Mommy ta kallesa tare da cewa. “A'a Naseer ka bari basai ka kaita ba ai zata shiga Napep”. Zare ido yayi tare da cewa. “A'a Mommy na isa kamar ni ace Matata tashiga Napep no, impossible kamar Matar Naseer Ibrahim ɗancanji amma ace Matata na hawa Napep Ina bai yiba bai yiba”. Ita kuwa Mommy aranta tace Ohhh wannan yaro dai Allah yamasa kurari bawai basu da arziƙinba mahaifinsa nadashi amman kurarinsa yafi kuɗin nasu yawa bashi da aiki sai cika baki. Khausar kuwa tuni ta fice cike da takaicin zumuɗinsa. Da sauri yabi bayanta yana cewa. “My dear Wife ki tsaya mana let me drop you”. Banza Khausar tayi masa tayi ficewar ta. Kashe murya yayi tare da cewa. “Dan Allah ki tsaya mai yasa kike yin haka?”. Ba tare data juya ba kana cikin ɗaure fuska tace. “A'a Uncle Naseer ka bari kawai zanje da kaina gidansu Asma'u nefa Napep ma zan shiga”. Murmushi yayi kana yace. “Yawwa muje kinga nima sai ingaishe da Umminta kinga dama na daɗe banga Asma'u ba yau ya kamata mu gaisa”. Khausar kam sake ɗaure fuska tayi tare da cewa. “Yaya Naseer Allah da kabari kada in saka wahala nasan baza ka rasa abinyi ba”. Langwaɓar da kai yayi tare da marairaice fuska kana ya karyar da murya tare da cewa. “Please My dear Wife allow me to escort you kinsan dai Ina ƙaunarki sannan ina son kasancewa da ke banaso kidinga nesanta kanki daga gareni”. Siririn tsaki taja aranta kana tayi gaba abinta domin har ga Allah zalamarsa na bata tsoro. Shi kuwa da sauri ya nufi Parking space tare da ɗaukar motarsa yazo ta gefenta tare da buɗe mata kana ya karyar da murya tare da cewa. “Please Wife to be kishigo mana”. Dai dai lokacin da gate man ya buɗewa Lamiɗo da Gimbiya Dadu suka shigo bisa duk kan alamu daga asibiti suke anje duba lafiyar Idonta dan bayan ta fito hannunta na riƙe da ledan magunguna da kuma tambarin asibiti. Gimbiya Dadu kuwa tun da ta sauƙa daga mota Idanunta nakan Khausar ta wani kafeta da Ido tare da sake laɓenta na ƙasa. Khausar kuwa cikin rawan jiki da tsinkewar zuciya tayi saurin koma wa bayan Naseer zuciyarta na bugawa da mugun ƙarfi cike da tsoro take karanta duk wata addu'a da tazo bakinta. Murmushi Lamiɗo yayi tare da cewa. “A'a Nasiru ya dai ina zakuje kaida Mutuniyar taka?”. Cikin yanayin zumuɗinsa da rawan kai ya shafa ƙeyarsa tare da cewa. “Abbah zan kaita gidansu Asma'u ne dan banaso ta hau Napep”. Jinjina kai Abba yayi kana yace. “Yayi kyau Allah ya kiyaye hanya, Khausar sai kun dawo”. Kasa cewa komai Khausar tayi still tana tsaye bayan Naseer zuciyarta na cigaba da tsinkewa ganin har zuwa lokacin Gimbiya Dadu na Binta da ido burinta su haɗa Ido. Gyaran Murya Lamiɗo yayi kana yace. “Khausar shiga mota ku tafi”. Cikin sauri tace. “Toh Abba”. Kana ta fito daga bayan Naseer tashiga gaban motar. Kallon Gimbiya Dadu Naseer yayi kana yace. “Yafendo sai mun dawo”. Ya ida maganar tare da buɗe mazaunin Driver ya shiga kana yaja motar suka fice ahankali ya dai-dai ta hancin motarsa suka hau kwalta. Sai asannan ya juya ya kalli Khausar da fuskarta babu annuri kona misƙala zarratin zaman blutooth dake kunnensa ya gyara ajiyar zuciya ya saki yana bin ilahirin jikinta da kallo hannunsa ya kai tare da ranƙwafawa kanta zai riƙe yalwataccen sumar dake gefen wuyanta zai shinshina. Cikin sauri Khausar ta kauce tare da watsa masa wani kallo. Tsuke fuska yayi tare da marairaice murya kana yace. “Haba My Wife mai yasa zaki min haka kibari mana in sinsina gashinki naji wannan Sanyayyar ƙamshin da yake fita”. Sake tsuke fuska Khausar tayi tare da tura ƙaramin bakinta kana tace. “A'a nidai Yaya Naseer ka bari bana so”. Langwaɓar da kai yayi kana cikin wata murya mai ɗauke da zallan shauƙi da sha'awa yace. “Toh na bari ai yanda kike so haka za ayi hope dai kina sona?”. Ƙasa tayi da kanta tana wasa da zara-zaran yatsun hannunta amma ba tace komai”. Sake narkar da muryarsa mai ɗauke da zallan sha'awa kana yace. “Dan Allah kice kina ƙaunata ko zanji daɗi kinsan na daɗe ina dakon soyayyarki azuciyata, Khausar kece rayuwata bazan iya rayuwa idan babu keba kece muradin raina, kece fitilar dake haskaka rayuwata ina miki sahihiyar ƙauna wanda bana yiwa kaina”. Lumshe idanunsa yayi tare da kallon fuskarta zuwa ƙirjinta kana yace. “Kece wacce zuciyata keda burin kasancewa da ita, kece farin cikina muddin ban mallakeki amatsayin matata ba bazan taɓa samun nutsuwa ba, My Khausi saboda ke nadawo Nigeria ba dan keba wlh bazan dawo ba. Duk yawan kyakkyawawan matan dake India babu wacce ta burgeni ta kuma kwanta min arai sai ke duk kyawunsu kallon maza nake musu!”. Ita dai Khausar batace komai ba sai wasa da take da yatsun hannunta. Naseer kuwa karyar da murya yayi tare da lashe lips ɗin sa kana yana binta da wani shu'umin kallo ya lumshe Idanunsa tare da cewa. “Khausar inada burin mallakar ki ke kaɗai ce zaki iya sarrafani, akan shimfiɗata sannan ke kaɗai ce zaki iya bani farin ciki akan shimfiɗa ta”. Lokaci ɗaya Khausar ta sake haɗe fuska cike da takaici tarasa Meyesa Naseer yake mata wasu irin maganganu marasa kan gado. Al'amarin Naseer yafi kama da irin mayaudaran mazan nan na zamani. Shirune ya ratsa motar har suka isa ƙofar gidansu Ummi yayi Parking daga waje, Ahankali Khausar ta ziro ƙafanta da suka sha jan lalle. Dai-dai lokacin Asma'u ta iso. Ganin Khausar yasa ta faɗaɗa fara'ar fuskarta kana tace. “A'a Khausisi, Lelewal tawa”. Murmushi Khausar ta sakar mata tare da gyara zaman gyalenta kana tace. “A'a ina kika je?”. Asma'u na gyara wuyan hijabinta ta kalli Khausar tare da cewa. “Wallahi kitso naje”. Jinjina kai Khausar tayi kana tace. “A lallai dai kam”. Juyawa tayi ɓangaren da Naseer ke tsaye ya zuba mata ido ɗauke kanta daga garesa tayi kana ta mayar da kanta kan Asma'u tare da cewa. “Asmeey ga Uncle Naseer”. Sai alokacin Asma'u ta ganesa da murmushi afuskarta tace. “Laa Uncle Naseer Mutanen India fatan kazo lafiya. Khausar tace min kadawo toh Allah yatemaka”. Kai ya jinjina cike da Iyayi kana yace. “Wallahi na dawo amma fa saboda My Khausi nazo, ana ɗaura mana aure kuma zan ɗauki abata mukoma can”. Murmushi Asma'u tayi tare da kallon Khausar da ta tsuke fuska kana tace. “Toh Allah ya tabbatar mana da alkhairi”. Da sauri ya amsa da. “Ameen”. Khausar kuwa hannun Asma'u ta riƙe zasu shiga gida. Da sauri yace. “Ya dai haka My Khausar ba zaki tsaya mu ɗanyi hira ba?”. Ataƙaice ta girgiza masa kai tare da cewa. “A'a”. Shafa kansa yayi tare da lumshe idanunsa kana yace. “Toh ƙarfe nawa zaki koma gida sai inzo in ɗauke ki”. Babu walwala atare da ita tace. “A'a ba sai kazo ba Uncle Naseer zan koma”. Wani irin zare ido yayi tare da girgiza kai kana yace. “A'a My Khausi kar ki min haka. Ni dai ki faɗa min ƙarfe nawa zanzo ɗaukarki”. Ƙaramin tsaki taja aranta tare da cewa wannan mutumin ya fiye naci afili kuma juyawa tayi ta kallesa tare da cewa. “Toh ka dawo ƙarfe shida na Yamma”. Kai ya gyaɗa tare da cewa. “Toh shikenan My Wife sai nazo”. Ya ida maganar tare da shigewa motarsa yaja. Bayan sun shiga cikin gida Khausar ta juya tare da kallon Asma'u kana tace. “Ya dai naga kamar Ummi bata nan?”. Kai Asma'u ta gyaɗa tare da cewa. “Eh Ummi ta tafi gidan Innayi. Ni kaɗai ce sai Bashir dana bari yana mana gadin gidan shiyasa ma ana gama min kitson na dawo. Jinjina kai Khausar tayi kana tace. “Ayyah yayi kyau”. Kai tsaye Bedroom din Asmau suka shiga fridge Asma'u ta buɗe ta kawo mata drinks da Fruit. Kallon Friut ɗin Khausar tayi tare da zabga ta gumi. Zama Asma'u tayi daga gefenta cike da kulawa tace. “Ya dai Khausar tunanin me kike?”. Ajiyar zuciya Khausar ta saki tare cire gyalenta ta ajiye kana ta kalli Asma'u tare da cewa. “Ni wallahi lamarin Uncle Naseer ya fara damuna”. Asma'u na ninke hijabin data cire ta kalli Khausar tare da faɗin. “Mai yafaru?”. Ajiyar zuciya Khausar ta saki tare da lumshe Idanunta kana tashiga zayyanewa Asma'u abubuwan daya yima tun daga zuwansa har yanzu daya kawota kana ta ɗaura da cewa. “Asma'u Uncle Naseer yana bani tsoro abubuwan da yake gwada min sun fi kama dana mayaudara idan yana wani abun tamkar yana da wani nufi akaina, sannan yana yawan nuna zalamarsa akaina, ya rinƙa wani abu kamar maye!”. Dariya Asma'u tayi tare da cewa. “Wataƙil tsanananin son da yake miki ne kike ganin kamar haka, kinga tun kina ƙarama kamar da wasa ya fara ce Miki matarsa har gashi girma yazo wataƙil tsananin soyayya ne sannan kinga ya zauna a ƙasar da al'adun mu ba ɗaya dana suba kinga ƙasashen India wannan sai ahankali runguma da sumbata basu ɗauke shi abakin komai ba may be shiyasa kike ganin yake miki haka kuma kinga ai ya riƙa dole zaiso mace”. Ajiyar zuciya Khausar ta sauƙe tare da furzar da iska mai zafi kana tace. “Anya kuwa Asma'u abin nasa is too hight ɗazun fa agaban Mommy saura kaɗan ya rungumeni saida na kauce”. Dafe kunci Asma'u tayi tare da kallon Khausar da fuskarta ke ɗauke da alamun damuwa kana tace. “Toh tunda har haka ne ki kiyaye al'amarin sa”. Ajiyar zuciya Khausar ta saki tare da lumshe Idanunta kana tace. “Zan kiyaye insha Allah amma gaskiya ya fara bani tsoro baki ɗaya al'amarin sa azalamance yake”. Jinjina kai Asma'u tayi tare da cewa. “Amma duk da haka yana sonki”. Kai Khausar ta gyaɗa kana ta buɗe Idanunta dake lumshe tace. “Na sani Uncle Naseer na ƙaunata, amma kuma wani lokaci soyayyar tafi kama da Sha'awa”. Girgiza kai Asma'u tayi tare da cewa. “No Khausar kada ki fassara shi da haka, sannan kinga yanzu lokaci yayi da zaki bawa Uncle Naseer dama kinga dama ga Maganar da Hajja Nana tazo da ita cewa kina gama Secondary school za ayi batun Aurenki kinga yanzu munzo gangara koma ince mungama kawai”. Shiru Khausar tayi tare da lumshe Idanunta tana jin wani iri azuciyar ta. Asma'u ta cigaba da cewa. “Sannan kin gani tayi miki maganar Yayanki Aliyu idan har baki amince da Naseer ba kika fitar dashi amatsayin wanda kike soba dole Yaya Aliyu za'a liƙa miki, kuma kinga Yaya Naseer tunda ansan Asalin sa sannan ansan komai nasa, kuma ke kanki kinsan yana masifar sonki”. Ƙaramin tsaki Khausar taja tare da kallon Asma'u kana tace. “Kayya Asma'u Asalin nasa har wani kyau gareshi!? Mahaifiyarsa fa ƙanwar Gimbiya Dadu ce Uwar su ɗaya ubansa ɗaya, kuma duk ɗabi'u da hallayar Gimbiya Dadu babu wanda mahaifiyarsa ta bari, sannan kuma shine ɗan Auta wajenta Ni Wallahi tsoron su na nake ji wallahi nama fi tsoron mahaifiyarsan”. Ajiyar zuciya ta sauƙe kana ta cigaba da cewa. “Amma shi Uncle Naseer bashi da matsala Saboda zuciya nason mai kyautata mata, shi kuma tun ina ƙara ma yake nunawa kowa cewa. Ni ta da bance ni ta musamman ce awajensa, na ɗaukesa ne tamkar wani sashina amma banjin Uncle Naseer awani mataki na daban sannan batun Yaya Aliyu kuwa gaskiya saidai Hajja Nana tayi duk abinda zatayi, amma ni bazan Aure shiba babu ta yanda zanyi na aureshi”. A hankali ta furzar da iska mai zafi daga bakinta kana ta kalli Asma'u da itama ita take kallo. Idanunta ta lumshe cikin sanyi murya tace. “Ni inaji azuciya ta ina da muradin da nake da ita na, musamman da nake buƙata inada muradin da nake so Asma'u ina da wani abun da nake so, wanda ni kaina bansan menene ba. Amma Uncle Naseer ba irin Nature da nakeso ajikin namiji yake dashi ba dama yanada ilimi Addini kamar Yah Jameel ne to da ya tsarkaka, dama ace ɗabu'unsa irin na Yah Jameel ne da ya cikemib ko wanne gurbi”. Ajiyar zuciya Asma'u ta sauƙe kana tace. “Allah ko?”. Tayi mgnar a fili yayinda zuciyarta ke saƙa wasu zantukan, ita kuwa Khausar kai kawai ta gyaɗa mata. Cikin sauƙe numfashin Asma'u tace. “Allah ya mana zaɓi mafi alkhairi dai”. Cikin lumshe ida Khausar tace. “Amin”. Hira suka cigaba dayi, ƙarfe biyar dai-dai Khausar ta miƙe tare da ɗaukan gyalenta ta yafa kana ta kalli Asma'u tare da cewa. “Asma'u Ni zan tafi”. Saurin Kallonta Asma'u tayi tare da cewa. “Toh ba kince sai ƙarfe shida zaki tafi ba?,Kuma ina Uncle Naseer zai zo ya ɗauke ki!?”. Baki Khausar ta taɓe kana tace. “Guduwa zanyi kafin yazo ɗin dai, ai shiyasa nace masa shida kinga yanzu biyar zan tafi”. Murmushi Asma'u tayi tare da cewa. “Toh idan yazo fa?”. Ka faɗa Khausar ta ɗage tare da taɓe baki kana tace. “Sai kice masa na tafi”. Ta ida maganar tana ficewa da sauri. Asma'u tabi bayanta dan yi mata rakiya. Misalin ƙarfe shida saura kwata Naseer yayi Parking aƙofar gidansu Asma'u tare da danna Hong. Asma'u dake sauraran zuwansa ta sanya hijabi ta fita zaune ta samesa acikin mota kana tace. “Bata daɗe da tafiya da taga iska ya taso”. Kai ya gyaɗa tare da cewa. “Nagode”. Kana ya figi motarsa yabar layin kai tsaye gidansu Khausar ya nufa lokacin daya isa ankira maghariba direct masallaci ya wuce ya gabatar da sallah kana ya wuce gidan kai tsaye sashen Gimbiya Dadu ya shiga. Shigarsa ba daɗewa Haiydar ya shiga bakinsa ɗauke da Sallama kana ya gaishesu tare da ajiye kulan abincin Gimbiya Dadu. Har ya juya zai fita. Naseer ya kallesa tare da cewa. “Please Haiydar kace da Khausi tazo zamuyi hira”. Kai Haiydar ya gyaɗa kana yace. “Toh Uncle Naseer sannan ya fita”. Kai tsaye masallaci ya wuce sai Misalin takwas saura kwata ya koma sashen su bakinsa ɗauke da Sallama. Khausar dake zaune kan 1sitter sanye cikin Neavy blue riga da wando na bacci mai santsi wanda ya sauƙa har ƙasa rigar kuma mai hannun Spaghetti ne kanta sanye da hular Net jikinta na fitar da sanyayyan ƙamshin tularen ta yayin da hannunta ke riƙe da wayar Mommy tana latsawa. Da sauri Haiydar ya kalleta tare da cewa. “Addah Khausar na manta ban faɗa miki ba, ɗazu kafin na wuce Masallaci Uncle Naseer yace. In faɗa miki kije ki same shi a sashen Gimbiya Dadu yana son ganinki”. Nanda nan Khausar ta canza fuska tare da cewa. “A falon Gimbiya Dadu kuma!?”. Harara Mommy ta watsa mata kana tace. “Toh cin yeki Gimbiya Dadu za tayi ko kuma me Ni nalura wani shan ƙamshi kike yiwa Naseer fa, idan kinsan bakya sonshi ki fito fili ki faɗa, sannan ki fito da wanda kike so, tun kafin kakar ki tazo ta buwayemu da batun Aurenki. Kinga dama ta ajiye target ne kina gama Secondary school magana ya ƙare za azo ayi miki aure”. Ajiyar zuciya ta sauƙa kana ta cigaba da cewa. “Idan kuma kinƙi baki da hujjar da zaki ƙi Auren Aliyu, dole kibi zaɓin ta dan haka ma gwara ki tsaida zuciyarki kisan me kike ciki don in duniya duk zasu taru babu mahluƙin da zai hana batun wai kin gama secondary School za'ayi miki aure, tunda har Hajja Nana ta rantse, dan haka gwara kawai ma ki tsaida zuciyarki, ki fidda mijin da zai iya barinki kici gaba koda kinyi aure, kuma da fidda wanda kike sone, zamu samu hujjar nuna mata kinada wanda kike son”. A hankali Khausar ta janye idonta daga kallon Mommy kana tace. “To amma ni gaskiya ba zanje. Falon Gimbiya Dadu ba”. Ɓata fuska Mommy tayi babu walwala atare da ita tace. “Maza ki wuce kije idan ita kura ce to ta cinye ki”. Miƙewa Khausar tayi badan ranta yaso ba sai dan ganin yanda Mommy ta ɓata rai yasa ta ɗauki hijabinta dake fitar da ƙamshi sanya kana ta fice. Acan ɓangaren su Moddibo kuwa zaune suke aɗakin Innayi shi da M Jameel bayan sun kammala cin abinci Anutse ya miƙe tare da kallon Innayi da suke magana da M Jameel ya gyara tsayuwar sa tare da cewa. “Innayi saida safe”. Kallon sa M Jameel da mamaki afuskarsa yace. “Zaka je ka kwanta fa kace?”. Kai Moddibo ya gyaɗa tare da lumshe idanunsa kana yace. “Eh”. Kai M Jameel ya gyaɗa tare da faɗin. “Ok nima zan tafi gida”. Ahankali Moddibo ya buɗe Idanunsa dake lunshe kana yace. “Mu kwana anan mana tunda har ƙarfe takwas tayi”. Girgiza kai M Jameel yayi tare da miƙewa kana yace. “A'a ina so Inje gida”. Kallon yanayin fuskarsa Moddibo yayi tare da cewa. “Dan Allah mu kwana mana”. Ataƙaice M Jameel yace. “A'a tafiya zanyi”. Ajiyar zuciya Moddibo ya sauke tare da cewa. “Toh shikenan ni zanje in kwanta”. Ya Ida maganar tare da ficewa. Da kallo Innayi da M Jameel suka bisa har ya ɓacewa Kallonsu. Moddibo kuwa yana shiga falonsa yayi saurin yarfe hannunsa tare da jan tsaki tare da jan numfashi kamar wanda yaci yaji lokaci ɗaya lips ɗin sa suka kama rawa cikin yanayin damuwa ya dafe kansa tare da cewa. “Ya salam³,Wannan wani irin al'amari ne meke mai wuyar ɗauka haka?”. Cikin mutuwar jiki ya wuce kichen tare da ɗaukan Cup ya ɗauraye ya zuba ruwan Tea kana ya yanka lemun tsami ya matse sannan ya zuba zuma ya kafa kansa ya shanye tass, ajiye Cup ɗin yayi ya fita zuwa Bedroom ɗin sa yana shiga ya kwanta ko minti ɗaya baiyi da kwanciya ba yayi saurin miƙewa ya zauna cikin sauri ya sake komawa ya kwanta tare dayin ruf da ciki cikin wani irin yanayi yasanya hannunsa duka biyu ya danne mararsa saboda wani masifaffen harbawa da yakeyi. Acan ɓangaren Gimbiya Dadu kuwa cikin sanyi jiki Khausar ta buɗe ƙofar falon tare da Sallama tana shiga ta...! *Littafin SAKAYYAH na kuɗine ƴar uwa ki biya ki karanta cikin Aminci da salama babu haƙƙin kowa a kanki littafin 1k ne kacal 0661110170 GTBank AISHA ALIYU GARKUWA sai ki turo min shaidar biyanki ta WHATSAPP 09097853276, kana in saki a Group ɗin da zanke posting nashi, yar uwa koda kinga LITTAFIN SAKAYYAH A WAJE TO na satane, in dai kin san baki biya kadama ki karanta.* *GARKUWAR* taku ce dai MA'AURATA, da masu shirin aure, da masu jego, da yan gayu masu son k’amshi kece raini, da gyaran da zaike maimaita muku dararen forkon kuruciya* Ko kunsan Jikinmu na da sinadaran hormones da suke taimakawa dan’adam akan komai musamman lokacin da mace take mu’amalar aure da mijinta. Mafi akasari wannan hormones din ne ke samun matsala ko su yi sanyi koma su daina aiki kwata-kwata shi ne dalilin da zai sa mace tace bata jin sha’awa ko bata san dadin aure ba. Albishirinku ina da kayan da ke taimakawa wannan sinadaran du dawo aiki tukuru don karkato miki da kimarki wajan mai gida sannan su taimakawa wannan sinadaran hormones dinki su dinka secreting din ni’ima wadatacciya da zata taimaka miki ki gamsu mijinki ya gamsu fiye da tunaninki. Note: Kayana ba sa tsinka ruwan ni’ima suna dai taimakawa hormones dinki ne su tsattsafo da ni’imar musamman wacca cutar sanyi ko dattin mahaifa ya dankarar da su ya hana su yin aikinsu yanda ya kamata. Haka zalika idan kina da kyau ki kara da wanka. Zaki iya amfani da magani na na gargajiya wanda zai gyara miki sex hormones din kullum ki kasance cikin humidify wato cikin damshi mai albarka kamar yanda ake son mace. Yana gyara miki mara. Sai kamshi. Hajiyata daure ki fara amfani da turarena ki ji irin salon kamshin sa salo ne da zai daidaita ki da mijinki ya kankaro miki da kimarki a wajansa. Siyan na gari mayar da kudi gida. Ga masu buƙata ga number' wayata wanda nake whatsApp dashi 09097853276 kimin mgn ta whatsApp in har kin tabbatar kin shirya saya mu dai-dai ta, kayana ba ƙanana bane, shiyasa bana harkan karanta, muddin kinsan baki shirya sayaba Please kada kiyi min mgn ki bari sai kin shirya kuɗinki a hannu, ba ina nufin kayana bana talaka bane, no akwai ƙananan set na masu karamin karfi, banson aimin mgn a ɓatamin lokacin aiyukana a shirme baki shiryaba. Shine karantan da bana so. 0005388578 Jaiz bank AISHA GARKUWA ALIYU. In kin shirya ga number ta ga kuma account number ta wanda in mun gama mgn zaki turo kudin ki, kana insa miki kaya a mota, duk ƙasar da kike kayana zaije gareki, amman fa in kinada dalilin zuwan nasune🤝🏻sayan na gari meda kudi gida. GARKUWAR MA'AURATA *By* *GARKUWAN MARUBUTA* [24/07, 6:14 AM] Halimatu A/rahman Sadeeya: Isreg'o. Cikin tsananin tsoro da mamaki Baba mai gadi ya juya gabas da yamma,r kudu da arewa acikin coumpund ɗin gidan amma babu mutum babu dalilin mutum, cikin tsananin kaɗuwa da ganin wannan abin al'ajabin yace. “Innalillahi wa'inna Ilahi rajiu'n. Cikin abinda bai wuce second ɗaya ba ace babu rago babu dalilinsa, kuma abu ayanke bawai da ransa ba bare ace ya gudu”. Cikin kaɗuwa ya nufi cikin gidan tare da cewa. “Ya Ilahi mai ya faru”. Duk ya burkice ganin abin yake tamkar mafarki dai-dai lokacin da mai gidan ƙanin Lamiɗo yake fitowa. Aruɗe Baba mai gadi yace. “Alhaji ragunan biyu suna ɗaure amma yanzu naga ba ɗaya”. Kallon Mamaki Alhj Musa ya masa tare da cewa. “A'a ragunan biyu yanzu kuma babu ɗaya ƙafa ragon yake dashi Malam Idi?. Aruɗe Malam Idi yace. “Wallahi tallalahi Alhj da gaske yanzu-yanzu ragonan yana nan amma yanzu ya ɓace babu shi babu dalilinsa”. Tsayuwa Alhj Musa ya gyara tare da cewa. “Toh ragon ƙafa zaiyi ina zai shiga?”,. Malam Idi daya gama shiga tashin hankali yace. “Wallahi da gaske Alhj”. ya faɗa tare da juyawa ya fice daga gate ɗin ganin su Khausar basu yi nisa ba yasa ya saki Ajiyar zuciya tare da cewa. “Khausar!, Khausar!! Kuzo”. A tsorace Khausar da Asma'u suka jiyo atare kana suka haɗa baki wajen faɗin. “Ya dai Baba mai gadi”. Hannu ya ɗaga musu tare da cewa. “Kuzo dai”. Cikin rawan jiki da tsoro Khausar tace. “Lafiya?”. Cikin ƙasa da murya Asma'u tace. “Mun shiga uku kad dai ya gane?”. Da ƙarfi Khausar ta haɗiye wani abu mai ɗaci tare da cewa. “A'a Insha Allahu ma bai gane ba”. Suna isa bakin gate ɗin yace. “Khausar kushigo”. Ƙara sa shiga sukayi zuciyar su na bugawa da mugun sauri. Kallonsu Baba mai Gadi yayi tare da kallon Alhj Musa kana yace. “Dan Allah dan Annabi ba ragunan biyu suna nan ba, har kuka tsaya kusa dasu suna ɗaure ba?”. Atsorace Khausar ta gyaɗa masa kai kana Muryanta na rawa tace. “Eh”. Da sauri Baba mai gadi ya sake kallon wajen tare da cewa. “Kawai ina zaune fa kamar abin wasa kamar amafarki kamar a Tv naga rago ɗaya ya ɓace”. Khausar da jikinta ya fara rawane tace. “Ya ɓace kuma?” Cikin tashin hankali Asma'u da Idanunta sukayi zuru-zuru ta dafe ƙirjinta tare da faɗin. “Ya ɓace kuma dai?”. Jinjina kai Baban mai gadi yayi tare da cewa. “Wallahi kuwa kun fita kenan ina juyawa naga ragon nan ya ɓace Khausar abin nan abin mamaki fa ina kuma kun gansu?”. Shi dai Alhj Musa na tsaye ya harɗe hannunsa aƙirji yana sauraransu cike da al'ajabi. Cikin tsananin tsoro mamaki da al'ajabi da kaɗuwa gami da kiɗima Khausar ta kalli Alhj Musa kana tace. “Wallahi kuwa Baba ƙarami muma munga ragunan nikam mafa akusa dasu na tsaya. Innalillahi wa'inna ilahi rajiu'n yau mun shiga uku Meye faru ya akayi haka?”. Jin hayaniya yasa mata dake cikin gida suka fara fitowa suna tambayar abinda yafaru duk wanda yaji rago ya ɓace sai yashiga cikin mamaki da al'ajabi. Baba mai Gadi da abin ya tsaya masa arai ya kalli mutanen dake wajen tare da cewa. “Wallahi ganin Idona ragon nan ya ɓace ɓat kamar a Film kuma babu kowa a farfajiyar gidan Khausar suna fita abin ya faru ina juyawa naga sun ɓace ɓat!”. Atsorace Khausar ta jinjina kai tare da cewa. “Wallahi kuwa Muma yanzu muka gansu mun samu ragu nan nan aɗaure”. Ana haka Mommy tashigo nan ta samu labarin rago ya ɓace nan suka shiga jajantawa. Khausar kuwa hannun Asma'u taja suka fice bayan sun fita Asma'u ta juya ta kalli Khausar tare da cewa. “Khausar”. Juyawa Khausar tayi tare da haɗiye wani abu mai Masifar ɗaci tace. “Asma'u”. Asma'u taja dogon numfashi kana tace. “Khausar da kece zaki ɓace fa. Innalillahi wa'inna Ilahi rajiu'n”. Khausar kuwa da jikinta yake rawan jitayi Idanunta sun ciko da hawaye cike da alhini tace. “Asma'u mun shiga uku”. Cike da rawan jiki suka ƙarasa gida kai tsaye ɗakin Khausar suka nufa tare da zama a ƙasa Capet ɗin duk sunyi zuru-zuru dasu kallo ɗaya zaka musu kasan cewa suna cikin ɗimuwa da tashin hankali mara misaltuwa. Cikin rawan murya Khausar ta kalli Asma'u tare da cewa. “To yanzu kam Uncle Naseer me yake nufi dani? Dama tsafi zaiyi dani, kenan Uncle Naseer ma tsafi ne Asma'u? ba kingani ba dama ni sam ban yarda da shiba, tsoronsu nake dama Gimbiya Dadu ya take bare kuma ƙanwarta mun shiga uku dama tsafi zaiyi dani Asma'u shikenan da kashe ni suke sonyi?”. Cikin raunin murya Asma'u tace. “Khausar wannan abin ya gigita ni na rasa ta yanda zan fassara shi”. Ta gumi sukayi yayin da zuciyarsu ta cigaba da bugawa tsoro da tashin hankali ya bayyana atare dasu lokacin ɗaya zazzaɓi ya fara dirarwa Khsusar. Ba jimawa Mommy ta dawo kai tsaye ɗakin Khausar ta shiga tana cewa. “Ohhh Allah mai iko an duba fa ƙasa da sama babu ragon nan babu dalilinsa an duba ko ina babu shi ya ɓace!”. Murya na rawa Asma'u tace. “Mommy muma fa mun gansu”. Mommy kuwa ahankali ta maida kallonta kan Khausar da jikinta ke rawa duk ta ruɗe cike da kulawa tace. “Khausar ya dai?”. Kuka Khausar ta fashe dashi tare da yarfe hannu kana tace. “Mommy zan faɗa miki Mommy zan faɗi gaskiya”. Kallon Mamaki Mommy tayi mata kana tace. “Meya faru Khausar?”. Cikin kuka sosai Khausar tace. “Allah Mommy Zan faɗi”. Zama Mommy tayi gefensu kana tace. “Wai meke faruwa ne Asma'u”. Cikin ƙoƙarin tsaida hawayen Khausar ta riƙe hannun Mommy acikin nata, kana ta zayyane mata duk yanda sukayi da Naseer da kuma shawarar da Asma'u ta bata sannan ta ɗaura da cewa. “Mommy kuma nice ɗazun na dandala ƙyallen akan wuyan ragon, har muka ji tsoro kar Baba mai gadi ya ganmu kuma Allah wanda na shafawa ƙyellen ne ya ɓace”. Aruɗe Mommy ta saki salati tare da sanar da ubangiji. _“Innalillahi wa'inna ilahi rajiu'n. Hasbunallahu wani'imal wakil. La'ilah ha Illah anta subhanaka Inni kuntu Minal Zhalimin. Allahumma Ajirni fii musibati wa'ahlifli khairan minha_. Ohh Khausar am nashiga uku wannan rayuwa har ina Khausar kin tabbatar?”. Kai ta gyaɗa tare da faɗin. “Wallahi tallahi Mommy da gaske ne”. Ta faɗa tare da cusa hannunta ƙarƙashin gado ta ciro mata ƙyallen data ajiye da niyyar idan Naseer yazo zata bashi”. Cikin raunin murya tace. “Mommy kingani Mommy kin gani ko wallahi shine ƙyallen”. Jinjina kai Mommy tayi tare da kallon ƙyallen da ƙamshinsa ke bugun kanta kana tace. “Nashiga Uku ni Aysha wannan masifa har ina?”. Asma'u kuwa ta gumi tayi ganin abin take tamkar almara. Khausar na share hawaye tace. “Mommy ina dai yanzu kin gani kinga zahiri Mommy inaga yanzu kam zaki iya yarda su Mayu neko?”. Girgiza kai Mommy tayi cike da jimami da kuma al'ajabi ta kalli Khausar tare da cewa. “Toh su sukayi ko shi Allah am nashiga uku ba'a shaidar halin ɗan mutum”. Girgiza kai Asma'u tayi kana tace. “Nikam wallahi Uncle Naseer ya bani Mamaki duk da rawan kansa ban taɓa zaton zai aikata irin wannan abin ba”. Ta gumi Khausar tayi duk abin duniya ya isheta Hausawa sunyi gaskiya da suka ce Mutum mugun Icce. Ganin yanda suka ruɗe da al'amari yasa Mommy dai-dai ta nutsuwarta tare da cewa. “Kar ku damu ku cigaba da addu'a domin addu'a takobin mumunice, sannan kada ku faɗa wa kowa wannan maganar ya zama sirri atsakanin mu”. Sai kuma ta maida kallonta kan Asma'u kana tace. “Asma'u Allah ya miki al'barka, kin cika ƙawar kirki duk inda ake neman ƙawar arziki kin kai. Allah Ubangiji ya Al'barkanci rayuwar ku ya kuma kare ku aduk inda kuke”. Haɗa baki sukayi wajen faɗin. “Ameen”. Ajiyar zuciya Mommy ta sauƙe kana tace. “Wannan magana ya zama sirri atsakanin mu, kada ku fadawa kowa daga. Ni sai ku sai kuma Ubangijin daya halluccemu shi kuma Naseer zamu ga manufarsa. Za muga iya gudun ruwansa sannan daga yau Khausar koda ya kira ki baza ki sake zuwa inda yake ba ko dai kina son shi!?”. Zaro ido Khausar tayi cikin sauri ta shiga yarfe hannun tare da Girgiza kai kana tace. “Allah Mommy bana sonshi, na tsane shi bani bashi har abada, me zanyi da matsafi ni dai bana sonshi Wallahi bana sonshi”. Kai Mommy ta gyaɗa tare da kallon su kana tace. “Toh shikenan ki kwantar da hankalin Allah ya tsare ku ya muku zaɓi da maza na gari, wannan ma ai addu'a ce tasa asirinsa ya tonu Allah ya ƙara tsaremu baki ɗaya ku kara riƙo da addu'a in sha Allah duk sharrin mai sherri sai dai yaga gadon bayanmu”. Atare suka amsa da. “Ameen”. Haka dai akayi suna aka watse kowa na al'ajabi da ta'ajjadin ɓacewar ragon suna. Acan gidansu Moddibo kuwa M Jameel zaune tare da Innayi Moddibo kuwa na tare da Malam Arɗo bai dawo ba. Anutse M Jameel ya ɗago kansa tare da kallon Innayi dake zaune ta tanƙwashe ƙafafunta cikin sanyin murya yace. “Innayi”. Ahankali ta ɗago kanta tare da cewa. “Na'am”. Ajiyar zuciya M Jameel ya sauƙe kana yace. “Innayi ni ko badan kar kice ina bincikar ki da tuhumar kiba. Da zance da Allah Innayi ina ne asalin ƙasar ku tunda nan dai garin naji labarin zuwa kuka yi dan Allah Innayi ki faɗa min inane asalin garinku sannan, wai kwata-kwata mahaifin A.J bashi da dangi ne? Sannan Ina dangin Mahaifiyarsa”. Ido Innayi ta tsira masa tana jin bugun zuciyarta na ƙawura. M Jameel kuwa cigaba yayi da cewa. “Sannan dan Allah kiyi haƙuri kada ranki ya ɓaci shin ke kakarsa ta wajen auwace ko kuma kakar sa ta wajen Uba ne?”. Kallonsa kawai Innayi keyi tana jijjiga ƙafarta. Ajiyar zuciya M Jameel ya saki kana yace. “Dan Allah Innayi ki faɗa min ina son insan wannan abin kada ki ƙi faɗa min ke ta wani gefe ne kika kasance. Kaka agaresa sannan kuma akwai abubuwa da dama da suke ɗaure min kai ina so insan su Innayi, idan har baki faɗa min suba Wallahi zan rayu da ƙumfa dan Allah ki faɗa min kada in mutu baki faɗa min ba”. Sanyayyar Ajiyar zuciya ta sauƙe tare da kallon M Jameel kana tace. “Aaa to mutuwan nan Kam Jamilu am ai tana kan kowa, sannan ni tsohuwa ma ban ce kar in mutu ban faɗa muku ba, sai kaine zaka ce kar ka mutu ban faɗa maka ba!”. Langwaɓar da kai yayi tare da karyar da murya cikin son karya logonta da batun zai mutu dan yasan bata son jin hakan yace. “Ni dai ki faɗa min”. Girgiza kai tayi tare da cewa. “Jamilu bana son tone-tone ne Jamilu abar kaza cikin gashinta fa yafi, sannan kuma babu amfanin tone-tone da faɗe-faɗe!”. Zamansa ya gyara tare da cewa. “Innayi Ni dai inaso shi tone-tonen nan da faɗe-faɗen nan ina so afada min waye ne A.J Ina son insan Abu akan Abokina kuma Aminina ina so insan komai akanshi”. Sauƙe numfashi tayi tare da kallon M Jameel kana tace. “Toh nayi maka al'ƙawari ni kuwa zan sanar maka da komai in. Allah ya yarda zan faɗa maka abinda ya sawwaka duk da cewa bakomai zan faɗa maka ba”. Jinjina kai yayi kana yace. “Toh Innayi nagode amma ranan yaushe zaki faɗa min”. Shiru tayi alamar tunani sai kuma tace. “Duk ranan dana shirya zan faɗa maka sai kazo kai kaɗai”. Jinjina kai yayi tare da cewa. “Toh shikenan Innayi Nagode sosai”. Bayan sun sake taɓa hira ne ya mata Sallama ya tafi. Da daddare Misalin ƙarfe takwas Naseer ya shiga gidansu bayan yaje ya gama sharholiyarsa kai tsaye falon mahaifiyarsa ya nufa zaune ya samu Mahaifiyarsa da Yayunsa mata guda biyu dawowarsu daga gidan sunan kenan basu daɗe ba. Zama yayi tare da gaishesu suka amsa cikin sakin fuska. Aunty Hindu ce ta kallesa tare da cewa. “A'a yau fa mun ga abin al'ajabi agidan Yaya Musa kawai ragon suna ya ɓace bat. Ni dai gaskiya ban yarda da mai gadin nan ba da ƙyar idan bashine ya sace ragon ba yazo yana ihu da kururuwa wai rago ya ɓace rago zai ɓace shi tsuntsune ko abin tsafi ne?”. Dariya Naseer yayi tare da kallon Addar tasa kana yace. “Atoh ku dai bin ciki mai gadin nan rago zai ɓace haka nan ba dalili ne”. Aunty Larai tace. “Atoh abin dai akwai abin dubawa”. Miƙewa Naseer yayi tare da miƙa yace. “Bari na shiga ciki na watsa ruwa”. Kallonsa Aunty Hindu tayi kana tace. “Bari muje ka bani tsaraba ta da yake baka da kirki tunda kazo ba kaje gida na ba Naseer”. Zaro ido yayi kana yace. “Wallahi ranan naje Aunty Hindu akace min wai kinje kitso yara basu faɗa miki ba?”. Kai ta gyaɗa tare da cewa. “Ai kuwa sun faɗa min ba shakka na tuna toh muje ka ban tsara bata”. Ta faɗa tare da miƙewa gaba yayi tabi bayansa har suka shiga tsarerren falon nasa da komai na ciki ash colour da baƙi ne Bedroom ya wuce Aunty Hindu kuma ta zauna aɗaya daga kujerun cikin falon tana jiransa. Naseer kuwa yana Shiga Idanunsa suka sauƙa akan yankekken rago Atsakiyar gadonsa Atsorace yaja baya cikin kiɗima da ruɗewa ya dafe kansa tare da furta. _“Innalillahi Wa'inna Ilahi rajiu'n”_ Aunty Hindu kuwa jin Muryar sa Aƙiɗime yasa ta miƙe da sauri ta isa Bedroom ɗin Idanunta bai sauƙa ko ina ba sai kan ragon. Dafe ƙirjinta tayi tare da cewa. “Innalillahi ragon anan kuma?”. Cikin sauri Naseer ya sanya hannunsa tare da rufe mata baki kana yace. “Na roƙe ki Aunty Hindu Dan Allah ki rufa min asiri kada ki faɗa kada kiyi maganar”. Cike da mamaki da kuma tsoro tace. “Toh kenan Naseer kaine ka saci ragon?”. Kallonta yayi tare da cewa. “Kamarya in saci rago kamar wani almajiri. nima ganin sa kawai nayi akan gadona kamar yanda kika gansa”. Harara ta watsa masa tare da kallon ragon dake kan gadon kana ta kallesa tare da cewa. “Kai ka sace mana in ba Haka ba Naseer menene?”. Wani shegen kallo ya watsa mata da alamun ɓacin rai atare dashi yace. “Ba sacewa nayi ba idan ma satar zanyi ba zan saci mai raiba!? Ko ni matsiyacine da bazan iya saya ba, ko mun rasa wadatane a gidan”. Sai kuma ya saki Ajiyar zuciya tare da dai-dai ta Muryar sa yace. “Kawai dai akasi aka samu?”. Cikin rashin fahimta tace. “Kamar ya akasi aka samu?”. Ƙugunsa ya riƙe da hannunsa biyu tare da furzar da Iska mai zafi daga bakinsa kana yace. “Kawai an ɓata min aikina ne?”. Cikin rashin fahimta tace. “Aiki kamar ya?”. Dafe kansa yayi alamun gajiya kana yace. “Na haɗa ki da Allah da darajar Manzonsa, ni kar kiyi min tonon silili da tereren ban kaɗa dan Allah ki haɗiye wannan maganar ƴar uwa ki rufa min asiri wannan magana tsakanin mu ne kawai kin gansa magana ya ƙare”. Ajiyar zuciya ta sauƙe tare da faɗin. “Toh ka faɗa min menene sirrin?”. Girgiza kai yayi tare da cewa. “Ba zaki iya ɗauka ba”. Kallonsa tayi kana tace. “Ka faɗa min menene bazan iya ɗaukar ba?Abinda nasani Naseer idan ma maita ce duk mun tsotsa fa!”. Sake ɗaure fuska yayi kana yace. “Maita ku kuka tsotsa ni dai bana maita amma ina abin da yafi maita!”. Zaro Ido tayi tare da cewa. “Menene?”. Ajiyar zuciya ya sauƙe kana ya sake kallon ragon lumshe idanunsa yayi tare da cewa. “Bokana ne ya bani laƙani idan nayi aiki da al'adan mace zanyi kuɗi zanyi arziƙi mai tarin yawa da yake ba kisan kai bane shiyasa na bayar”. Cije labɓansa na ƙasa yayi kana yace. “Sannan kuma duk yarinyar data saka min jininta zan zo in same ta akan gado na”. Furzar da iska mai zafi yayi daga bakinsa kana yace. “Aunty Hindu ina fama da matsala tun da nadawo ƙasar nan ban samu nayi Sex ba. Ina dame ina cikin tsananin buƙatar Mace, toh kinga Khausar kuma ina sonta sannan nasan cewa nizan aureta shiyasa na bata mahaɗin maganin da aka bani ƙyallen akan ta samin jininta kinga da ita zanzo in samu akan gado madadin ragon nan". A hankali ya numfashi kana ya cigaba da cewa. “Kinga zanyi Sex ɗina da ita baza ta hanani ba kana nasan. Ni zan aureta shiyasa ban damu ba jini kuma ba wani abu zai mata ba kawai dai in Anyi amfani da jinin zanyi arziƙi ne, zan shiga cikin manyan Yara na wannan ƙasar sai dai kiji ƙanin ki ya zama yaro da kuɗi abokin manya, kije Makka kije Madina inkai ki Dubai in kaiki India kije duk ƙasar da kike so afaɗin duniya”. Cike da takaici Aunty Hindu tayi Ƙwaffa tare da cewa. “Shegiyar yarinya ta ɓata mana aiki, ai wannan yarinyar da kake gani dama ba a abin arziƙi da ita, kai dai ka dage kana sonta ne amma da wata yarinya ka samu wawuya sai ta saka maka amma wannan da shegen wayo kamar dila, kaga duk yanda akayi jinin ragon ta saka ajiki tunda dai kaga rago ne yazo maka kan gado”. Jinjina kai yayi tare da cewa. “Wallahi kuwa”. Dafa kafaɗar sa tayi tare da cewa. “Kada ka damu zan nema maka yanda zakayi kayi aikin nan”. Kai ya gyaɗa kana yace. “Toh shikenan Aunty Hindu. Amma fa muyi taka tsantsan tunda mukayi na farkon nan ya wargaje ina tsoro ko kuma kawai ma zanje in samu Bokan nawa ya canza min sabon salon aiki”. Kallon sa tayi tare da cewa. “Amma kana ganin hakan zai yi?”. Kai ya jinjina mata kana yace. “Sosai ma dama ya bani zabi biyu ne akwai wanda za'ayi amfani da jini, sannan idan inaso akwai wanda za'ayi amfani da Sparm ɗina amma matsalar nan duk yaran garin basu waye bane dake ba wani babban gari bane ba zaiyi kaje ka hakewa yarinya ba kuma ma anfiso na matata toh akwai kuma na maciji sai dai shi sai Bayan anyi aure ne, kuma yafi muni shiyasa bana sonshi amman gsky zaifi bada manyan kuɗaɗe”. Cije lips ɗinsa yayu tare da cewa. “Da zan samu nayi Sex ai zan iya saka Sparm ɗina ayi aiki da shi dan boka yace anfi son sama amma nace ayimin dana Period ɗin saboda zanci riba bibbiyu kinga zan samu in kashe ƙishin dake damuna, zan samu inyi da Khausar tunda Ni zan aureta, sannan kuma mahaɗin arziƙi na zaiyi”. Ajiyar zuciya Hindu ta sauƙe kana tace. “Shikenan kaci gaba da gwadata idan ta yarda da lallami in kukayi sex din ai shikenan”. Jinjina kai yayi tare da cewa. “Toh zan gwada hakan”. Atake awajen ya ɗauki ragon yakai kichen sannan ya daddatsa yasa abako kana ya miƙawa Aunty Hindu ya ce. “Ki tafi dashi”. Dariya tayi tare da cewa. “Wato dai munci banza”. Murmushi yayi kana yace. “Eh sosai ma munci banza, to mun isa mu fita da ragon munce mun sameshi adakina ne, aikinga asirinmu zai tonu". Jinjina kai Hindu tayi kana tace. “Hakane”. Kai tsaye gidanta ta nufa da ragon zata gyara musu kamar yanda yace. Wayewar garin Laraba baki ɗaya Jama'ar Garin Gembu sun tashi da lumshi tun ranan da akayi ruwa tamkar da bakin ƙwarya da kuma rugugi ba asake yin ruwa ba kusan Makonni biyu kenan garin ya zamana har sun fara ɓuƙatar ruwa duk da irin sanyin da ake musu amma garin ya fara ɗumi ga hadari daya haɗu baƙi asama sai dai babu ruwa sai Sanyayyar Iska mai sanyi da ratsa jiki da ake surarawa. Acan ɓangaren Khausar kuwa cikin shiri ta fito daga Bedroom ɗin ta cikin riga da wando na Pakistan daga saman rigar atsuke take yayin da daga ƙasanta kuwa abuɗe take wando kuwa Pencil ne sosai kayan suka amsheta sai ya fito tamkar Kajol yayin data ɗaura Maroon ɗin hijab har ƙasa jikinta na fitar Sanyayyar ƙamsin turaren Oud Ma'arup bakinta ɗauke da Sallama tashiga Bedroom ɗin Mommy. Anutse Mommy ta ajiye Carbin dake hannunta kana tace. “Har kin shirya?”. Kai ta gyaɗa tare da cewa. “Eh Mommy”. Ajiye Carbin Mommy tayi tare da kallonta kana tace. “Khausar ki kula koda Ummin Asma'u bana so ku faɗa wa abinda ya faru”. Kai Khausar ta gyaɗa kana tace. “Toh Mommy ni dai nasan da ƙyar idan Asma'u ta faɗa wa Ummin ta amma idan ma ta faɗa mata shikenan dan nasan Ummi koda ta faɗa mata babu matsala”. Jinjina kai Mommy tayi tare da ciro 1k A pose ɗin ta tace. “Ga Kudin transport”. Amsa Khausar tayi tare da faɗin. “Nagode”. Kana ta fice. Tana fita ta tari A dai-dai-ta Sahu ta shiga tafiyar minti ashirin da biyar ne ya kaisu gidansu Asma'u. Anutse ta sauƙa tare da bashi kudin kana ta tura ƙaramin gate ɗin gidan tashiga tare da nufar falon bakinta ɗauke da sallama tashiga Ummi dake zaune a falo ta faɗaɗa Murmushin fuskarta tare da cewa. “Khausar sannu da zuwa”. Cike da ladabi Khausar ta tsugunna tare da cewa. “Ina Yini Ummi?”. Murmushi Ummi tayi tare da faɗin. “Lafiya lau Khausar yasu Hajiya Aysha dasu Haiydar?”. Khausar ta amsa da. “Lafiya ƙalau suna gaisheki”. Jin muryan Khausar yasa Asma'u dake Bedroom din Ummi tana gyara fitowa da murmushi afuskarta tace. “Fattanah”. Miƙewa Khausar tayi tare da wurga mata Harara kana tace. “Ai wannan sunan na barwa wanda ya liƙa min shi amakaranta sai dai kuma ya sawa wata amma ba dai niba abi wani sarkin”. Dariya Asma'u tayi kana tace. “Ai Suna linzami tunda wasu ma idan za'a kwana ana ce musu Khausar basu sani ba sai ance Fattanah kinga, kuwa Yaya Moddibo ya sanya miki suna ya biki ko ba ragon suna”. Taɓe baki Khausar tayi kana suka shiga ɗakin Ummi atare suka gyara ko ina tare da jona bona suka sa turare. Bayan sun gama gyara ko ina suka koma ɗakin Asma'u. Ajiyar zuciya Khausar ta sauƙe cikin ƙasa da murya tace. “Asmau'u kin faɗa wa Ummi Maganar?”. Girgiza kai Asma'u tayi tare da cewa. “Wallahi ban faɗa mata ba Khausar ai Mommy ta gargaɗe mu”. Jinjina kai Khausar tayi tare da kallon Asma'u kana tace. “Asmeey kin kuwa san har yau Naseer bai sake zuwa wajena ba sannan bai sake yi min magana ba. Kuma wayar daya bani akwai sim card da komai da komai amma har yanzu bai sake kira na ba”. Girgiza kai Asma'u tayi tare da faɗin. “In dai bai miki maganar ba kada kiyi masa. waya kuma kima ajiyeta kawai dan kuɗin san nan bama asan na menene ba, kana bamusan me yake nufi dake ba”. Tagumi Khausar tayi har yanzu abin na mugun bata mamaki koda wasa bata taɓa tsammanin Naseer zai mata haka ba. Asma'uce ta riƙe Hannunta kana tace. “Waya sani ma ko Lalata yayi niyyar yi dake yanda ragon nan ya ɓace wataƙil ke ki ɓace tema ma aɗakinsa za'a sameki yayi rapping ɗinki”. Lumshe idanu Khausar tayi kana ta buɗe su akan Asma'u tare da sauƙe Ajiyar zuciya kana tace. “Haka ma Mommy na tace kuma kinga ta karɓe wayar ma sannan ta tura asiya min waya acikin Taraba wayar da yafi wacce ya kawo min ma za'a siya Min”. Muskutawa Asma'u tayi kana tace. “Yama fi miki nima Ya Jameel yace zai siya min waya”. Wara Ido Khausar tayi cike da farin ciki tace. “Kice mun kusa muyi waya mu daina Aron na su Ummi”. Jinjina kai Asma'u tayi kana tace. “Ai dai Lallai kam munji daɗin mu”. Acan ɓangaren Moddibo kuwa a hankali ya fito da motarsa daga gidan Malam Arɗo ya dai-dai-ta hanci motarsa akan titi cikin nutsuwa yake driven yayin da ƙira'ar ke tashi acikin suratul Muminin cikin, Sanyayyar sautin muryarsa yake bin ƙira'ar dai-dai ƙofar gidan su M Jameel yayi parking tare da ciro wayarsa yayi dearling number M Jameel Amma har ya katse ba ayi Picking ba sake kira yayi still ba amsa ajiye wayar yayi tare da buɗe Murfin motar kana ya fita mai gadi naganin sa yayi saurin miƙewa hannu Moddibo ya bashi suka gaisa ahankali Moddibo yace. “J yana ciki ne”. Cike da girmamawa mai gadin ya girgiza kai tare da cewa. “A'a” godiya Moddibo ya masa kana ya shiga motarsa kai tsaye gidan Ummi ya nufa da tunanin ƙila Jameel na can bayan yayi Parking ya fito Anutse ya shiga Falon bakinsa ɗauke da Sallama. “Ummi dake zaune tana Azkharul masa ta ɗago kai tare da faɗada fara'ar dake fuskarta kana tace. “Babana sannu da zuwa”. Cikin yanayin nutsuwarsa da kuma sanyinsa yace. “Ummi ina yini”. Ta amsa da. Lafiya tare da tambayar Innayi Kansa a ƙasa yace. “Duk suna lafiya Ummi J fa?”. Zama Ummi ta gyara tare da cewa. “Tun shekaran jiya da kuka zo ai be sake zuwa ba amman dai nasan in sha Allah yau zaizo”. Ajiyar zuciya Moddibo ya sauke kana yace. “Ayyah ni kuma tun safe da muka rabu bamu haɗu bane shiyasa nazo nan, naje can gidan Abba ma baya nan nayi tsammanin ma yazo nan wataƙil ko suna tare da Innayi”. Shiru Ummi tayi alamar tunani kana tace. “Eh to wataƙil ma yana can”. Jingina kai Moddibo yayi kana yace. “Ni na kira ma baya ɗagawa”. Hannu Ummi ta miƙa tare da ɗaukar wayarta kana tace. “Bari na gwada”. ta faɗa tare da dearling. Cikin sa'a yana shiga M Jameel Yayi picking tare da Sallama. Ajiyar zuciya Ummi ta sauƙe kana tace. “Ina kake ne?”. Anutse M Jameel yace. “Ummi ina wajen Innayi ce muna hira”. Kallon Moddibo tayi tare da faɗin. “Aikuwa ga Moddibo yazo neman ka”. Dariya M Jameel Yayi kana yace. “Rabu dashi Ummi be nemeni agida ba ya tafi maƙota yana nema na”. Kallon Moddibo dake sakin ajiyar zuciya Ummi tayi kana tayi murmushi tare da cewa. “Ai dai kam”. Moddibo kuwa kallon Ummi yayi bayan ta katse wayar yace. “Toh Ummi bari na tafi tun da yana gida kam”. Jinjina kai Ummi tayi kana tace. “Toh ba matsala Moddibo Nagode bari na kawo maka abin taɓawa”, Ta faɗa tare da miƙewa kichen tashiga tare da ɗauko masa Alkaki da dambun naman kaza ta ajiye masa acikin wasu roba masu kyau. Amsa yayi da faɗin. “Nagode Ummi”. Sannan ya juya har ya isa ƙofan Falon Ummi tayi saurin cewa. “Yawwa Babana tsaya dan Allah ka ajiye min yarinyar nan agida”. Ta faɗa tare da juyawa ta nufi ɗakin Asma'u tare da cewa. “Khausar ina yanzu zaki tafi ga Maghariba ta kawo kai?” Daga ciki Khausar ta ɗan daga sautin muryanta tare da cewa. “Eh Ummi yanzu zan tafi”. Kai Ummi ta gyaɗa tare da juyawa kana tace. “Toh ki fito Yayanki ya sauƙe ki tunda dai dole sai yabi ta titin unguwar ku”. Murmushi Khausar tayi tana ƙoƙarin sanya hijabinta tace. “Yaya Jameel ko?”. Cikin sauri ta fito falon Cak ta tsaya ganin Moddibo nanda nan ta nemi fara'ar dake fuskanta ta ta rasa. Hannunta Ummi ta riƙe kana tace. “Yawwa Babana ka sauƙe min ita agida kasan ƴaƴa mata bama so suna kaiwa dare awaje”. Shiru Moddibo yayi tun lokacin da Ummi ta ambaci sunan Khausar ya nemi nutsuwarsa ya rasa sam baya. Son wata alaƙar da zai haɗa sa da yarinya. Jin yayi shiru Ummi ta kallesa tare da cewa. “Ya dai Babana ko dai da matsala ne?”. Girgiza kai yayi kana cikin sanyin murya yace. “A'a”. Still tana riƙe da hannun Khausar tace. “Toh dan Allah kayi haƙuri ka sauƙeta aƙofar gidansu Lamiɗo”. Jinjina kai yayi tare da faɗin. “Toh shikenan Ummi”. Sannan ya fice. Har jikin mota Ummi da Asma'u daketa murmushin mugunta suka raka Khausar. Anutse Moddibo ya buɗe mazaunin Driver ya shiga Khausar kuwa cikin tsinkewar zuciya ta buɗe gaban motar ƙiran Rang Rover tashiga cikin sauri ta lumshe Idanunta jin wani ƙamshi mai daɗi daya ratsa hancinta ne yasata lumshe ido, ahankali ta tukure jikinta waje ɗaya. Moddibo kuwa motar yaja. Hannu Ummi ta ɗaga musu tare da cewa. “Toh Allah ya kare Babana Nagode Allah Yamaka albarka”. Asma'u kuwa murmushi kawai ta saki ganin yanda Khausar tayi tsuru-tsuru tamkar za'ace ƙyat ta arta da gudu. Tunda suka shiga motar babu wanda yace da ɗan Uwansa komai kowa da irin tunanin da yake Aransa kana ga abin hawa da suke giftawa da ɗan gudu kasancewar maghariba ta gabato Ahankali Khausar ta juya tare da satan kallon sa gudun kada tayi laifi awajen sa yace bata gaishesa ba yasa cikin sanyin murya tace. “Malam ina yini”. Banza yayi da ita kamar bai jiba. Cikin sanyin Murya ta sake cewa. “Malam ina yini”. Still banza ya mata. Lumshe Idanunta tayi akaro na uku kana tace. “Malam ina yini”. Still ƙin tanka ta yayi ya cigaba da Driving ɗinsa. Ƙawar da kai gefe Khausar tayi tare da watsa masa Harara kana ta murguɗa baki asaman laɓɓanta tace. “Ai dai nafita hakki ko awajen Allah”. Shi kuwa Moddibo tunda wannan abin yafaru atsakaninsu yasa yake jin haushin Yarinyar gani yake tamkar idan suka haɗu zata rainasa kana yana ganin yanayin da suka kasance Amafarki kamar ta sani. Cikin dakekkiyar murya yace. “Idan kika sake tura min bakin nan, zan tsike lips ɗin in watsawa karnuka”. Tsit tayi kamar bata cikin motar, mamaki kawai takeyi ya akayi yasan ta murguɗa mishi baki, domin ko ta inda take bai kallaba. A haka dai sukaci gaba da tafiya. Suna cikin tafiya wata Trailer tazo ta hannun damar su yayin da wata ƙaramar mota ke gefen hagunsu daga gabansu kuwa mai Napep ne duk ajere suke tafiya Trailer dake gefen damar su ya yanko ta gefensu tamkar zai hau kansu cikin sauri Moddibo ya karkatar da kan motar zuwa hagunsa cikin rashin sani ya gogawa motar dake hagunsa cikin sauri ya juya akalar motar zuwa gaba nan ma ya bugi mai Napep dake gabansu gaba ɗaya abun ya faru a lokaci ɗaya kamar ƙibtawar ido. Cikin tsananin tsoro da kiɗimar ganin accident na Shirin faruwa yasa Khausar ƙwalla ƙara tare dasa hannunta kan hannun Moddibon ta damƙe fam tare da faɗin. “Innalillahi wa'inna Ilahi rajiu'n, Ɗiyyyyttt-ɗiyyyytttt”,Tayi ƙaran tare da hayewa jikin Moddibo ya zama na duka rabin jikinta na kansa kana ta ƙanƙame hannunsa tare da manna kanta adamten sa na dama. Har lau kuma Ɗiyyyt-Ɗiyyyyyyt take cewa kamar itace motar. *Littafin SAKAYYAH na kuɗine ƴar uwa ki biya ki karanta cikin Aminci ba haƙin na kanki, 1k ne kacal 0661110170 GTBank AISHA ALIYU GARKUWA sai ki turo min shaidar biyanki ta WHATSAPP 09097853276 sai in saki a Group na inda nake posting littafin. In dai baki biya sis kada ki karanta min littafina, kuma in kin gashi a wasu wuraren ma na satane, na Allah ya isa.* Cikin sauri mai Napep ɗin ya ƙara gudu wancan motar tabi bayansa,Cikin ikon Allah ya zamana babu wanda yaji ciwo Ajiyar zuciya Moddibo ya sauƙe yana sakin numfashi baki ɗaya ya gama Imagine zai haw kan mai Napep ɗin nan, baki ɗaya zuciyarsa ta tsinke. Khausar kuwa numfashi ta shiga saukewa akai-akai tare da sake manna kanta ajikin damtsen hannunsa. Ahankali ya juya ya kalli yanda rabin jikinta ke kansa cikin wata Sanyayyar murya mai cike da wani irin yanayin salo yace. “Sake ni”. Wannan shine karo na biyu arayuwarsa da yaji yayi amfani da irin wannan murya wanda shi kansa bai san daga inda ya samo shi ba. Ita kuwa cikin sauran tsoron tayi lamo a jikinsa. Buɗe idanunsa yayi da kyar murya a harɗe yace. “Zaki kasheni fa”. Haka nan taji raunin muryar da yayi mgn da ita har tsakiyar kanta. Cike da tsoro da kuma sanyin jiki ta janye jikinta daga garesa kana ta sauƙe ajiyar zuciya cikin rawan murya tace. “Ni dai ka sauƙe ni anan zan shiga Napep”. Harara ya watsa mata kana ya cigaba da Driving ɗin sa batare daya tanka taba yana isa ƙofar gidansu yayi Parking cikin sauri ta buɗe Murfin motar ta fita Shikuwa kai tsaye gida ya nufa, zuwa lokacin har anfara kiran sallar maghariba yana Parking ya fito cikin nutsuwa ya nufi sashen sa tare da wucewa yashiga toilet kana ya ɗaura alwala ya fito dai-dai lokacin da M Jameel ma ya fito daga ɗaya ɗakin da alamun shima alwala yayi. M Jameel na Kallonsa ya zuba masa ido yana murmushi kana yace. “No wonder A.J Ashe ƙwarjininka ba halitta kaɗai bace gadone jinine mai ƙarfi ke yawo a jikinka”. Anutse Moddibo ya juya tare da kallon M Jameel daya tsaresa da Ido kana yace. “Meye kake kallona haka?”. Murmushi M Jameel Yayi kana yace. “Ina kallon kane tamkar...! *Al'bishirunku Ma'aurata, GA GARKUWAR KU nan tafe muku da tsarabobi na musamman gareku ma'aurata daga cibiyar mgnin mata mai taken GARKUWAR MA'AURATA* NI DAI AYSHA ALIYU GARKUWA. Ina matukar mamakin wani irin lokaci da ya riske mu mai wahalallan fassara. Kullum dai magana daya ce, akan ma’aurata, fada, rashin jituwa, mutuwar aure, akan kuskure kalilan, rashin kula, rashin yi wa juna uziri. Toh wai duk me ya janyo hakan? Na zurfafa a tsananin tunani hakan ya tilasta min bincike mai tarin yawa wanda ya kai ni ga gano inda matsalar take? Shin yar’uwa ke macece amma kin san wacece mace ku? Kin san me ake kira mace kuwa? Mace ita ce matar da take zama iyali a wajan namiji ta zame masa bango, sanyin idaniyarsa, ta zame masa gata da farin cikin rayuwarsa ta zame masa ruwa abar kore ƙishinsa ta zame masa mayafi mai karesa daga gigitar kadaice, ta kuma dorar da mijinta kan turbar gaskiya, ta kashe masa jiki da salonta ta rikita shi da baiwa da ni’imar da Allah ya bata idan har ta san hanyar mayar da kanta sabuwa dal awajanta, wato kullun takasance masa tamkar amarya har ya kasa tantance daren amarcinsu da sauran dararen rakun rayuwar su. Wannan ita ce mace. Ina da wata saukakkar hanyar da zaki zama abar so da kulawa da soyayya a wajan mijinki ta hanya mafi sauki, 09097853276 hanyar ita ce ki gwada amfani da kayana na gyara ki gani, ina mai tabbatar miki da in sha Allahu sai kin dara da murna sai kuma kin gode min. Kayana kaya ne da aka yi shi da zallan itacanmu na gado marasa illa a cikin jikin dan adam musamman mace, kaya ne da suke taimakawa (sex hormones 😍) dinki. Misali kina kallon India😘, hollywood, Asian film🥰 kina ganin yanda mazansu ke nunawa matansu tsananin soyayya kamar su ba su kyautar ransu!? Saboda me hakan? Saboda suna sadaukar da lokacinsu wajan gyara jikinsu da kayan da ke tsattsafo da ni’ima cike da tsukewa, kayan nan kuma ana yinsu ne zallar magungunan gargajiya wanda ba su da illa domin haɗine na ingantattun itatuwa da yayansu. Ina baiwar Allahn da miji ke daure mata fuska babu hirar arziki? Zo ki ji yar’uwa zan baki gumbata da zallar gari wanda aka yi su da nagartattun itacen da ke da matukar amfani a jikin mace. Gubar ciko, gumbar tsalle dole, gubar da ba'a baiwa mai kishiya, garin maɗi, garin mallaka, tsumin goron tula, tsumin tsartai, tsumin maratsi, pala-pala butar sirri, kwanon k’asaitacciyar mace, furar mata madararta gareki Hajia takenta sha yanzu mgni yanzu, Ina mata masu fama da sanyi? Sanyin mara ki zo na hadaki da magani na na sanyi wanda yake wanke mara ya fitar da duk wata cuta da ke samun mazauni a wajan. Ina da ciccibi mai kyau. Ina da hadin amare mai kyau wanda zai gyara yarinya ya kankaro mata kimarta akwai hadin mai jego wanda muke yinsa na asali inada kekkyawan Hadi maida tsohuwa yarinya. Akwai daya bangaren wato *KAMSHI* Kimarki gyaranki da kamshinki. Matan da suka gane suka san yanda za su kankaro da mutunci su ne masu amfani da kayan gyara da kuma sanyaya jikinsu da kamshi, ina da turaren wanka da na bandaki na daki na jiki da na kaya dana tsuguno kamshin turarena na dabam ne mai sanyaya zuciyar wanda ya shaka ina da kayan kamshi na amarya da na maijego da na uwargida da dukkan macen da take kokarin mayar da kanta mai daraja a idon kowa ta zamo sarauni a idon mijinta, akwai shu'umar humra, sayan na gari maida kuɗi gida, banda karanta yayin gyara Hajia. Zaku iya samun kayyakina a duk garin da kike, zakiyi min mgn ta whatsApp number na 09097853276 domin yin zaɓinki, ko karin bayani, zaki tura kuɗin ta account na 0005388578 Jaiz bank AISHA GARKUWA ALIYU in mun gama mgna zan sa miki kaya a mota yazo duk garin da kike, in baki shirya saya yanzuba Please kada mu wahal da juna ki bari sai kin shirya kafin kiyi min mgn. 🤝🏻🥰😘 Daga taku AYSHA ALIYU GARKUWA *(GARKUWAR MA'AURATA)* *By* *GARKUWAN MARUBUTA*[30/07, 1:40 PM] Halimatu A/rahman Sadeeya: Idrneɗɗ. Cikin sauri Moddibo ya katsesa tare da cewa. “Kana kallona kamar me?”. Murmushi M Jameel yayi tare da shafa sajensa kana yace. “Ina kallon ka kamar Ayu uban Jarababbun duniya”. Harara Moddibo ya watsa masa tare da cewa. “Mtssss kai dai baka da aikin yi”. Ya ƙare mgnar tare da yin ƙasa da kansa yana kallon yanda Jallabiyar, lumshe Idanunsa yayi lokaci ɗaya tsikar jikinsa ya tashi cije labɓansa na ƙasa yayi kana yaja siririn tsaki tare da komawa Bedroom ɗin sa buɗe durowarsa yayi tare da ɗaukar boxes ya sanya kana yaƙara dogon wando sannan ya fito still. Yana jin tudun A ɗin sa M Jameel na ganin fitowarsa ya juya suka fice kai tsaye Masjid suka nufa tare da gabatar da Sallar Maghariba basu fita ba sai da suka idar da Sallar Isha'i sannan suka fito. Bayan sun isa bakin gate M Jameel ya nufi jikin motarsa dake fake Kallonsa Moddibo yayi kana yace. “A'a Baza mushiga muci abinci ba?”. Cike da kulawa M Jameel yayi murmushi tare da cewa. “Aini naci tunda zafinsa, kasan tun yaushe muke tare da Innayi kuwa? tun bayan sallar la'asar muna tare fa sai da aka kira maghariba nashigo nan nayi alwala”. Wara Ido Moddibo yayi kana yace. “Iyee gulmar me kuka yi?”. Murmushi M Jameel yayi tare da faɗin. “Ta faɗa min komai ta faɗa min duk kan abinda baka sani ba”. Gyara tsayuwa Moddibo yayi tare da harɗe hannunsa aƙirji kana ya juya ya kallesa tare da cewa. “Kamarya abinda ban sani ba?”. M Jameel kuwa murmushi yayi tare da cewa. “Zuwa yanzu nafi ka sanin kan ka ma nafi ka sanin wanene kai duk yanda kasan kan ka to yanzu na fika sanin kan ka”. Lumshe idanu Moddibo yayi tare da shafa sashensa kana ya buɗe idanun nasan tare da kallon M Jameel yace. “Iyeeeeh toh zo ka fesa min mana tunda angumtsa maka na hannun damana”. Tsayuwa M Jameel ya gyara tare da cewa. “Sirrine sai da nayi al'ƙawari bazan fesa maka ba kafin ake fesa min”. Moddibo kuwa murmushi yayi tare da shafa sajensa kana yace. “Toh yanda kayi lallaɓa nima zanje inyi lallaɓan afaɗa min”. Cikin dariya M Jameel yace. “Toh kaje ka gwada sa'arka, amma yanzu kam kasani bana cikin duhu”. Taɓe baki Moddibo yayi kana yace. “Iyyeeee wato gulmana nema kuka tayi”. Agogon dake ɗaure atsintsiyar hannunsa ya kalla ganin da ɗan sauran lokacin salla ne ya juyo ya kalli Moddibo tare da faɗin. “Ba wani gulmarka da muka tayi na dai faɗa mata cewa kana ɓuƙatar aure yanzu”. Cikin sauri Moddibo ya juya tare da watsa masa Harara Dariya M Jameel yayi tare da buɗe motarsa yashiga mazaunin Driver key yayi wa motar tare da saita hancin motar ya fara tafiya. Shi kuwa Modibbo da ƙafa ya nufi masallacin. A hanya ya tsaya yayi salla kana ya ƙarasa cikin gidan. Parking aharabar gidan cike da nutsuwa ya fito tare da nufar falon bakinsa ɗauke da sallama ya shiga. Ahankali yake bin cikin falon da kallo batare daya shiga ba cikin hasken fari gloves ɗin da suka haska falon kana da murmushi afuskarsa yace. “Ina Umminaaaa?”. Ummi dake zaune kan 3sitter idanu ta zuba masa batare da tace komai ba. Malam Ahmad dake zaune kan 1sitter ya kalli M Jameel dake tsaye ƙofar falon tare da cewa. “Ƙara so mana Jamilu”. Juyawa yayi ya kalli Ummi kana yace. “Kin tsaresa da ido kuma baki ce masa ya shigo ba”. Murmushi M Jameel yayi tare da cewa. “Ummi nayi kyau ko?”. Jinjina kai Ummi tayi still Idanunta na kansa tace. “Sosai ma Babana”. Murmushi yayi tare da Wara ido kana yace. “Iyyeee naji daɗina yau kuma nine Babanki ko da yake Baban miji ai baba ne?”. Kai Malam Ahmad ya gyaɗa kana yace. “Sosai ma”. Ummi kuwa still Idanunta na kanshi. Bashir daya fito daga Bedroom ne ya kalli Ummi kana ya kalli M Jameel data tsirawa Idanu matsawa kusa da Ummin yayi tare da cewa. “Yaya Jameel wallahi Ummi na sonka kamar me”. Sai asannan Ummi ta ɗauke Idanunta daga kan M Jameel ta mayar kan Bashir tare da yi masa daƙuwa kana tace. “Haka naka Bashiru”. Asma'u data fitowarta kenan daga Bedroom tayi murmushi tare da zama gefen M Jameel. Miƙewa Malam Ahmad yayi tare da nufar ɗakinsa bayan sun gaisa da M Jameel. Kallon Asma'u M Jameel Yayi tare da cewa. “Asmeey”. Cike da ladabi ta ɗago kanta kana tace. “Na'am Yaya”. Ajiyar zuciya ya sauƙe tare da cewa. “Zuwa yanzu kaso 85% cikin 100% na nauyin ku dake araina nake tunawa 85% sun sauƙa min saura shabiyar nake tunawa 15% ɗin nan kuma sune manya masu wuya”. Ajiyar zuciya yauƙe tare da cewa. “Ina so inga kinyi karatu kin gama, sannan na miki zaɓi da miji na gari Mumini, Salihi, Mai tsoron Allah, na Aura masa ke, sannan na danƙa masa Amanar ki. Hakazalika Ina so inga Bashir ya gama karatunsa ya fara aiki ta yanda ko bana kusa zai kula da Ummin mu ba zata nemi komai ta rasaba”. Cikin yanayin damuwa Asma'u tayi ƙasa da kanta lokaci ɗaya Idanunta suka ciko da hawaye yayin da taji zuciyarta yana masifar bugawa da ƙarfi Allah ya sani in ta tuna zatayi aure ta rabu da Unminta tanajin ba daɗi. Cikin raunin murya tace. “Bare ma Yah Jameel kai zaka yiwa Ummi komai kafin mu”. M Jameel kuwa murmushi yayi tare da kallon Asma'u kana ya cije labɓansa na ƙasa tare da lumshe idanunsa yana sauraron bugun zuciyarsa ajiyar zuciya ya sauƙe tare da buɗe idanunsa akan Asma'u kana yace. “To ai ita rayuwar dama ta gaji haka watarana ayi farin ciki watarana ayi baƙin ciki!”. Girgiza Kai Bashir yayi tare da kallon M Jameel cikin yanayin tsinkewar zuciya ya gyara zamansa tare da cewa. “Yah Jameel Meyesa kake karyar mana da zuciya ne!?”. Girgiza kai M Jameel Yayi tare da kallonsu wani irin tausayinsu da kuma ƙaunarsu na ratsa dukkan zuciyarsa, bashi da wani ƙunci a rayuwarsa fiye da yadda ya kasance baya tare da Umminsa da ƙannensa a inuwa ɗaya, ciwon sakin mace ba iya kanta kawai yake tsayuwa ba, har kan ƴaƴan data haifa yake shafa. Iska mai zafi ya fesar daga bakinsa kana yace. “Ba karya zuciya bane Bashir burina ne, akan ku inaji kuma har yanzu akwai kason da ban idaba, sabida ban zaɓawa Asma'u mijin aure a shine babban abinda yafi damuna sannan kai kuma kagama makarantar ƙuruciya ce sai jami'a gidan kazo nazo”. Numfashi yaja tare da fesarwa Idanunsa nakan Bashir yace. “Acan ne ake samun tarbiyya daban-daban da halayyar al'ummar matasa kashi-kashi ina tunanin kada ginin da mukayi nida Ummi wani yaje yayi yaɓe akai ya lalata kyakkyawan gini da kyakkyawan tubalin da mukayi maka”. Da sauri Bashir ya jujjuya kai tare da cewa. “In sha Allah haka bazai faruba”. Cikin jin sanyi yace. “Bashir kayi min al'ƙawarin zaka kasance nagari, kayi min alƙawarin zaka kasancewa Ummi farin cikinta”. Lokaci ɗaya hawaye suka cika idanun Bashir cike da tsoron kalaman Yayan nasa. Cikin wata razananniyar murya ya kalli M Jameel da Idanunsa ke lumshe kana yace. “Nayi maka al'ƙawari Yah Jameel Nayi alƙawari zan kasancewa Ummi ɗa nagari zan kasance me share mata hawaye, zan kasance mai sata farin ciki idan Allah yayi duniya dan Manzo (S.A.W) ”. A hankali ya ɗaga idanunsa tare da kallon Ummi da ta tsirawa M Jameel idanu cikin wani irin yanayi ko ƙyaftawa bata yi ajiyar zuciya ya sauƙe kana yace. “Zan kasance mai sata farin ciki, nayi alƙawari Ummi ba zata taɓa shiga ƙunci ko damuwa ba in dai a kai nane in sha Allah”. Ahankali M Jameel ya maida kansa jikin kushin ɗin ya jingina kana ya miƙe ƙafafunsa tare da riƙe hannun Bashir aciki nasa kana ya cije lips ɗin sa. Ummi kuwa wani irin sanyi jikinta da zuciyarta keyi cikin wani irin yanayi ta zubawa M Jameel Idanu. Anutse M Jameel ya buɗe Idanunsa dake lumshe ya sauƙe akan Ummi Ajiyar zuciya ya sauƙe tare da furzar da iska daga bakinsa kana yace. “Ummi ya dai kike kallona haka kamar na ƙarshe!?”. Cikin saurin Ummi ta dafe ƙirjinta daya buga da ƙarfin gaske cikin raunin murya irin na wanda ke gab da zub da hawaye ta kallesa karo na farko arayuwarta data fara kiran sunan sa tace. “Haba haba Jamilu”. Cike da mamaki ya ɗago idanunsa da suka sauya launi ya kalleta, Asma'u ma da sauri ta kalli Ummi haka ma Bashir karo na farko kenan arayuwar su da suka ji Ummi ta kira M Jameel da sunan sa. Ummi kuwa lokaci ɗaya wasu hawaye masu masifar zafi suka fara bin kuncinta Shar-shar. Cikin yanayin tashin hankali M Jameel ya sauƙa tare da ƙara sawa gabanta ya durƙusa tare da riƙe hannun ta cikin sanyin murya yace. “Ummi kiya femin Ummina kiya femin kada ki zubar da hawayenki akaina Ummi me nayi miki!”. Damƙe hannunsa Ummi tayi cikin raunin murya da alamun tashin hankali tace. “Meyesa kake zuwa kake karya mana zuciya nida ƙannenka, kasani ayanzu kaine Inuwata kaine mafakar da muke samu nida ƙannen ka muke fakewa. Meyesa wasu lokutan idan kazo kake min wasu maganganu masu wuyar fahimta”. Ta ida maganar hawaye nabin kuncinta. Ajiyar zuciya ya sauƙe tare da yin murmushi yayin da Idanunsa ke sheƙi kana yace. “Toh Ummi inada ikon canza ƙaddarata ce? Idan son samu ne Ummi zan kasance me Kula dake har iya ƙarshen numfashi na, kuma zan kasance me saki acikin farin ciki da walwala har numfashina na ƙarshe”. Girgiza kai Ummi tayi still Hawaye nabin fuskarta tace. “Ko yanzu ka sanya ni farin ciki duk kan wani farin ciki da jin daɗi ka bani shi Jamilu”. M Jameel kuwa cike da mamaki ya ɗago Idanunsa dake jiƙe da ruwan hawaye yace. “Ummi me kika ce?”. Cikin Muryan kuka tace. “Jamilu nace”. Kallonta yayi cikin rawan murya yace. “Ummi Meyesa?”. Hawaye na zuba daga idanunta yayin da jikinta ke tsuma tace. “Toh me zance maka? Kana tunanin bana jinka araina ne? Kana zaton bana jinka ajikina ne? Ban taɓa ganin wani ɗa kafin kai bafa Jamilu, kaine ɗana na farko tsatsona, jinina, mallakina, kafin inga Asma'u da Bashir da dai abu ya sameka a ace ina da ikon canza ƙaddara da zan dawo dashi kaina, domin nasan ko bayan raina zaka kula da ƙannen ka fiye da yanda zan kula da su”. Sauƙe ajiyar zuciya tayi tare da share hawaye masu zafin gaske da suka zubo mata kana tace. “Kaga ma min komai Jamilu, kayi min komai Jamilu. Ubangiji Allah Yamaka albarka Allah Ubangiji ya rufa maka asiri duniya da lahira Allah yasa kagama da duniya lafiya”. M Jameel kuwa sake Matsawa jikin Ummi yayi tare da ɗaura kansa akan cinyarta hawaye masu zafin gaske suka shiga bin kuncinsa Shar-shar-shar. Ganin haka yasa Asma'u dake gefe ita hawaye suka shiga bin kuncinsa. Kusa da Asma'u Bashir ya matsa tare da sanya hannu ya shiga share mata hawayen cikin raunin murya yace. “Kiyi haƙuri Asma'u kada kiyi kuka kinga zaki ƙara karyarwa Ummi zuciya”. Kai ta gyaɗa yayin da hawaye suka cigaba da zubowa daga Idanunta cikin sheshsheƙan Kuka tace. “Ka gani fa Yah Jameel ma kuka ya keyi”. Jin haka yasa M Jameel da Idanunsa ke jiƙe da hawaye ya ɗago kansa tare da sakar mata da murmushi kana yace. “Hmmm Asma'u kinsan meyake sani kuka?”. Kai ta girgiza still Hawaye na bin kuncinta. Lumshe Idanunsa yayi tare da taune lips ɗin sa kana yace. “Kada kiyi kuka saboda ke baki da abinda zai saki kuka”. Cikin sheshsheƙan kuka ta kallesa still hawaye na zuba daga Idanunsa cikin wata raunan'niyar murya tace. “Toh Yah Jameel me yake saka kuka Idan muna da iko zamu raba ka dashi”. Girgiza kai yayi tare da rintse idanunsa kana yace. “Ba zai rabu ba Asma'u tun tasowa ta aduniya bayan shekara goma sha huɗu bani da damuwar data wuce ganin Ummi bata gidan mahaifina, hankalina yana tashi akan hakan, kuma ina tunanin hakane badan faɗa da ƙaddararta ba, a'a saidai inajin maraici inajin kewar ta, inajin ciwon rashi mahaifiyata a cikin gidanmu, ina so ko yaushe Idan na tashi naga Ummi kusa dani haka zalika idan zan kwanta ya zama naje gareta taimin addu'a muyi saida safe”. lumshe idonsa yayi yana mai jin wani irin yanayi azuciyar kana ya buɗe su tare da cewa. “Ina so kafin naje na kwanta akowani dare in ganta kafin naje nayi bacci ina jin kamar nayi rashin komai na duniya da Ummi bata kusa dani ina jin mai zan mata na sauƙe hakkinta na uwa akaina”. Shafa kansa Ummi tayi still hawaye nabin fuskarta kana cikin raunin murya tace. “Toh wai meye rage da bakayi min ba? Ka kaini Makka, Ka kai ni Madina ka gina min kyakkyawan muhalli ka zuba min Kyakkyawan kayan ƙawa, ka riƙe cina shana suturata jinyata nawa dana ƙannen ka harma mijin da nake tare dashi har maƙotan dake tare dani baka barsu sun zubda hawayeba kanai musu dukkan abin buƙata”. A hankali ta danne kukan dake ƙoƙarin sufce mata kana tace. “Jamilu har maƙota nafa kagama yi musu komai”. Murmushi M Jameel yayi still Hawaye na bin kyakkyawar fuskarsa kana yace. “Har yanzu ban gama ba Ummi, sai dai ki tayani da addu'a Allah yasa in gama Allah yabani ikon gamawa”. Sai kuma ya maida kallonsa kan Asma'u dake zubda hawaye har zuwa lokacin take kuka kana ya maida kallonsa ga Ummi yace. “Ina Son inga na Aurar da Asma'u sannan inga Bashir ya zama babban mutum magidanci kafin wannan lokacin Ummi *INA SON INYI AURE”*. Cikin sauri Ummi ta ɗago Idanunta dake jiƙe da hawaye ta kallesa kana tace. “Me kace Jamilu?”. Ɗago kansa yayi tare da kallonta kana ya jinjina mata kai tare da cewa. *“Ummi ina so inyi Aure”.* Cike da mamaki Ummi ke kallon aranta tace tunda nake arayuwarta Jameel bai taɓa faɗa min magana makamancin haka ba”. Sake Kallonsa tayu akaro na barkatai kana tace. Babana kaine? Kai da bakinka kake ce min kana so kayi Aure?”. Jinjina kai yayi tare da faɗin. “Ummi ina so inyi Aure in ɗaukeki ku dawo gidana dake da Malam sannan Asma'u da Bashir duk mu zauna tare dasu duk sanda gari ya waye na dawo gidana in ganki Kusa dani mu zauna afalonki ki bamu tea musha Idan dare yayi kafin na kwanta nazo na zauna afalonki ki bani Tea nasha”. Sauƙe ajiyar zuciya yayi tare da lumshe idanunsa kana ya buɗesu tare da cewa. “Sannan nayi hira da ƙanne na. Ina son haka Ummi shiyasa nake so nayi Aure Insha Allah Ummi zanyi Aure zanyi Aure”. Ummi kuwa cike da mamaki da kuma jin daɗin kalamansa tayi yalwataccen murmushi kana tace. “Haka naka”. Da sauri ya rufe idanunsa tare da cewa. “Ummi ni ɗin?”. Cikin shafa kansa tace. “Eh kai ɗin, wato dan kana son ka sanarmin zakayi aurene, sai kabi ka kashe min jiki, ka zauna ka tasani gaba harda kukanka, ko gaisawafa baka bari kunyiba, ashe du mgnar auren ce ke tsaburarka”. Murmushi Asma'u da Bashir sukeyi cike da jin daɗi, Shima M Jameel murmushi yakeyi tare da sunkuyar da kansa cike da alamun kunya. Ita kuwa Ummi numfashin jin dadi ta fesar tare da cewa. “Allah ya yarda Babana Ubangiji Allah ya nufa. Allah ya Al'barkanci rayuwar ka Allah ya nufa. Allah ya rufa maka asiri Allah ya maka kyakkyawan tanadi agidan Aljanna ya kuma yima zaɓi da mace ta gari”. Murmushi yayi cike da jin daɗin Addu'ar ta ya shafa sajensa tare da cewa. “Ameen Ummina”. Asma'u da Bashir kuwa dariya sukayi suna jin ƙaunar Yayan nasu, miƙewa yayi tare da yiwa Ummi Sallama kana ya fice bayan tayi masa Allah ya tsare. Kai tsaye gidansu ya nufa cikin nutsuwa yake Driving har ya isa gida bayan yayi Parking ya fito atsaye ya hango Abbansa akan barandar sashen sa ya goya hannunsa abaya. Ganin Abba yasa ya nufesa Ajiyar zuciya Abba ya sauƙe tare da kallon sa kana yace. “Babana daga ina haka kake?”. Langwaɓar da kai M Jameel yayi tare da sanyaya muryarsa kana yace. “Abbah daga gidan Ummina nake”. Numfashi Abbah ya fesar kana ya kalli agogon dake ɗaure atsintsiyar hannunsa tare da cewa. “Babana kalli fa yanzu ƙarfe sha ɗaya da rabi Meyesa baka tsoro ne”. Ajiyar zuciya M Jameel ya sauƙe tare da kallon Abba kana yace. “To Abba tsoron me Mutum zaiji, duk guduna fa bazan guji ƙaddarata ba haka zalika duk saurina ƙaddarata ta fini sauri, kana duk hamzarina da kuma ɓuyana ƙaddarata tafini sanin inda nake”. Jinjina kai Abba yayi kana yace. “Duk da haka bana so Babana, duk inda kake indai ƙarfe sha ɗaya yayi ka kwana awajen, ba wani abin ni na amince ma nasan ba baza kwana alalaceccen waje ba ko kuma inda zai jaza min magana”. Cike da ladabi ya jinjina kai kana yace. “Toh Abbana”. Kansa Abba ya shafa yace. “Ubangiji Allah ya Albarkanci rayuwar ka Allah yatsareka da duk kan abinƙi”. Murmushi yayi tare da faɗin. “Ameen Abbana”. Kana ya juya ya nufi ɗakinsa. Acan gidan Lamiɗo kuwa Hajiya Aysha ce zaune da ƴaƴanta acikin falon su. Ramadan dake zaune gefen Khausar ya ɗago kai tare da kallon ta kana yace. “Addah Khausi ke kam kin huta da zuwa makaranta”. Murmushi Khausar tayi tare da kallon Ramadan kana tace. “Yanzu zan fara wani ai Ramadan”. Ya mutse fuska yayi kana ya kalli Mommy dake zaune kan 2sitter yace. “Mommy na”. Ahankali Mommy ta ɗago kanta tare da cewa. “Na'am Ramadan ɗina”. Langwaɓar da kai yayi tare da marairaice murya kana yace. “Ayyah Mommy am gobe abarni kar Inje makaranta mana”. Kallonsa Mommy tayi tare da cewa. “Toh Meyesa Ramadan?”. Kai ya Girgiza kana ya marairaice murya tare da cewa. “Mommy nidai kawai bana son zuwa Makarantar nan”. Hankalinta ta mayar kansa kana tace. “A'a Babana ba yadda za'a yi haka ace baka son zuwa makaranta. Ai yanzu ka fara zuwa ma”. Araunace ya kalli Mommy tare da cewa. “Dan Allah Mommy Gobe kawai. Na goben nan dan Allah Mommy na kada Inje Mommy na goben nan kawai kada abarni Inje makaranta kada inje”. Girgiza Kai Mommy tayi cike da kulawa tace. “A'a Ramadan ya za'a yi inbarka ba kaje makaranta ba ai bazai yuwu ba dole ne kaje makaranta kam”. Jan zuciya yayi tare da dafe kuncinsa kana yace. “Mommy shikenan kin yarda in tafi?”. Jinjina masa kai tayi tare da cewa. “Na yarda mana kaje”. Miƙewa yayi daga wajenta ya koma kusa da Khausar tare da riƙe Hannunta cikin yanayin roƙo ya langwaɓar da kai tare da marairaice murya yace. “Addah Khausy ki tayani bawa Mommy haƙuri gobe kada Inje makaranta kice tabarni gobe kar Inje makaranta mu zauna da ita bana son zuwa makarantar nan Addah Khausi bana so ki faɗawa Mommy”. Khausar kuwa Kallonsa ta riƙa yi har ya kai ƙarshe, ajiyar zuciya ta sauƙe tare da riƙe tafin hannunsa acikin nata kana tace. “Toh Ramadan tun daga yanzun ka kana primary 3 sannan kace bakason zuwa makaranta Primary mafa yanzu kayi rabin gamawa ai Ramadan ka fara da wuri”. Araunace Ramadan ya kalleta tare da cewa. “Yanzu Addah Khausi zaki bari inje”. Cikin rashin ɗaukar maganarsa da muhimmanci Khausar tace. “Eh Sosai ma”. Haiydar dake kwance kan 3sitter ya ɗago kansa tare da kallon Ramadan kana yace. “Eh dolenka. Dolenka ma kaje”. Sai kuma ya maida kallonsa kan Mommy dake kallon Ramadan kana yace. “Allah Mommy Idan aka sakewa Ramadan ma bazai yi karatu ba”. Tura baki Ramadan yayi tare da sake hannun Khausar ya koma jikin Mommy kana yace. “Mommy ki faɗa masa ƙoƙarin da nake a hadda ai yasani ko. Gasa akaje ni nake zuwa mana na ɗaya a sate ɗin mu”. Jinjina kai Mommy tayi tare da cewa. “Na sani Ramadan kana ma da kokari kawai dai da kake cewa kar abari kaje gobe abarka ka hutane bai yi ba. Idan ka tuna ma gobe Laraba ne idan kaje gobe jibi Alhamis zaka huta gata Friday shima zaka huta kaji ko Ramadan”. Girgiza kai yayi still Idanunsa akan Mommy yace. “Ayyah Mommy ni Banason zuwa ki barni mana”. Khausar ne ta kallesa cike da mamaki tace. “Ohh Ni Khausar yau kam naga ikon Allah da nacin yaro”. Taɓe baki Haiydar yayi tare da cewa. “Rabu dashi duk zai gama kuma dole gobe sai yaje makaranta”. Acan Bedroom ɗin Hajiya Bunayya kuwa kwance take akan makeken gadonta daya ji shimfiɗa na alfarma kana kunnenta maƙale da babbar waya ta gyara kwanciyarta tare da cewa. “Nama gama ɗaukar wannan matakin in Allah ya yarda in dai wannan anyi angama ya wuce Babban shima Insha Allah za asan abinda za'a yi akai”. Daga ɗaya ɓangaren Hajiya Lami dariya tayi kana tace. “Da dai yafimiki in ba Haka ba kina gani ƴaƴan ki zasu zama bayi, dan da zaran sarautar nan ta fita ahannun ku kinyi bankwana da ita ƴaƴan ki kuwa sun zama tamkar ba ƴaƴan Sarauta ba, duk da cewa Masarautar ba wata babba bace ai baka so ya wuce kaba ya fita ahannunka!”. Ajiyar zuciya Hajiya Bunayya ta sauƙe kana tace. “Hakane”. Murmushi Hajiya Lami tayi tare da faɗin. “Kinga ai Gimbiya Fadeela ta cikin Taraba Aminiya tace duk iya ƙoƙari tanayi dan ganin sarauta ya zauna ahanununta ke kanki kinsani ai ina faɗa miki saboda iya na cinka iya samun abin ka”. Jinjina kai Hajiya Bunayya tayi kana tace. “Hakane ai ma duk na gama shi in faɗa miki”. Ajiyar zuciya Hajiya Lami ta sauƙe kana tace. “Ai haka yafi kam kada ki tsaya kallon ruwa kwaɗo ya miki ƙafa”. Dariya Hajiya Bunayya ta sheƙe dashi kana tace. “Kede ki bari zaki sha kallo”. Hira suka sake taɓawa daga haka Hajiya Bunayya ta katse kiran. Washe gari. Da safe baki ɗaya yaran aka shirya su cikin Uniform Bayan Khausar ta gama shirya Ramadan cikin Uniform ɗin sa tamiƙe ta shiga kichen dan ɗauko masa Lunch box ɗin sa. Ramadan kuwa yana ganin fitan cikin sanɗa ya fice daga sashen nasu zuwa sashen Hajiya Bunayya ya ɓoye. Khausar kuwa kai tsaye Bedroom ɗin su ta nufa bakinta ɗauke da Sallama Cak ta tsaya ganin Ramadan bai ciki ƙara sawa ciki tayi tare da kiran sunan sa amma shiru toilet da Wadrope ta buɗe still baya ciki. Cikin sauri ta fito tare da nufar Bedroom ɗin Mommy kana ta kalli Mommy dake zaune gefen gado tace. “Mommy na gama shirya Ramadan da Raudat kuma ga Raudat amma banga Ramadan ba har munje wajen mota bamu gansa ba”. Miƙewa Mommy tayi tare da cewa. “Ikon Allah to ina kuma yashiga?”. Buɗa hannu Khausar tayi da faɗin. “Allahu A'alam”. Falon suka fito tare da duba ko ina amma baya nan. Kallon Khausar dake leƙa bayan Kushin Mommy tayi kana tace. “Khausar jeki duba ɗakin Haiydar ko yaje ya ɓuya acan yau, Bansan meke damun Yaron nan ba tun jiya baya so ayi masa batun zuwa makaranta abinda bai taɓa yi ba”. Taɓe baki Khausar tayi kana tace. “Iyayi mana Mommy daga anyi masa wasa shikenan ya ɗauka”. Ta ida maganar tare da fita zuwa ɗakin Haiydar. Abakin ƙofan ta tsaya tare da ɗan ɗaga sautin Muryanta kana tace. “Ramadan kafito fa?”. Shiru ba amsa jin haka yasa ta buɗe ƙofar ɗakin tashiga shiru ba kowa da mamaki take kallon ko ina dake kimtse tsaf har toilet ta ɓude still baya ciki siririn tsaki taja tare da ficewa ta koma sashen Mommy. Ƙugunta ta riƙe da hannu ɗaya kana ta kalli Mommy dake tsaye tace. “Mommy ban gansa ba fa”. Girgiza kai Mommy tayi tare da faɗin. “Toh kije ki duba sashen Ummanku ko yaje ya ɓuya acan kinsan itama zata iya ɓoyesa”. Kai Khausar ta gyaɗa kana ta juya ta fice. Bakinta ɗauke da Sallama tashiga falon zune ta samu Hajiya Bunayya akan 1sittee. Kallon ta Khausar tayi tare da cewa. “Ummah Ramadan yazo nan?”. Murmushi Hajiya Bunayya tayi tare da gyaɗa kai kana tace. “Eh gashi nan yazo ya ɓuya wai yau baya son zuwa makaranta”. Ƙwaffa Khausar tayi kana tace. “Aikuwa dole sai yaje”. ta faɗa tare da wuce Bedroom Kana tace. “Wallahi Ramadan kafita idona”. Jin muryan Khausar yasa Ramadan miƙewa tare da hawa can karshen gadon Hajiya Bunayya kana ya ɗaga sautin muryansa tare da cewa. “Dan Allah Ummah ki hanasu kice yau dai kawai subarni kada Inje makaranta”. Murmushi Hajiya Bunayya tayi tare da haɗa hannunta biyu waje ɗaya kana tace. “Dole sai kaje maza ka fito ka tafi nikam kasan bazan hanaka zuwa makaranta ba, Ramadan dole zaka je”. Dai-dai lokacin Sulaiman ya fito tare da faɗin.. “Ikon Allah yau Ramadan da kanka kake cewa baka son zuwa makaranta duk ƙoƙarin kan nan?”. Shi dai bai ce komai ba Khausar na ƙoƙarin za gayawa gefen gadon ta riƙo sa yayi saurin ɗirƙa ta ɗaya side ɗin gadon ya fice waje da gudu. Dafe kai Khausar tayi tare da bin bayansa yana cewa. Ramadan kazo mu tafi Sulaiman duk sun shiga mota saura kai ka ɗai ake jira”. Shi kuwa Ramadan sashen Mommy ya nufa da gudu yana shiga ya ɓuya abayan Mommy. Muryarsa na rawa tamkar wanda ke shirin fashewa da kuka yace. “Mommy dan Allah kar inje”. Hararansa Mommy tayi kana tace. “Sai kaje Meyesa ba kason zuwa Ramadan ka faɗa min dalili”. Rau-rau da idanunsa yayi kana yace. “Ni dai bana so bazan jeba Mommy”. Dai dai nan Khausar ta shigo kansa ta nufa tare da miƙa hannunta da niyyar kamasa tayi saurin damƙe maranta tare da rintse Idanunta kana tace. “Wayyo Allah na!”. Cike da kulawa Mommy ta kalleta tare da cewa. “Yau kuma ciwon cikin ki ko?”. Kai ta gyaɗa mata cikin sanyi murya ta kalli Ramadan kana tace. “Ramadan kazo mana kai kaɗai fa ake jira”. Maƙale kafaɗa yayi dai-dai nan suka jiyo hong ɗin mota cikin sanyin murya Khausar tace. “Mommy kin jifa shi kaɗai ake jira zasuyi letti fa Allah zaija idan sunje azanesu kinsan, Moddibo ba ruwansa ko yara sawa yake aci ƙaniyarsu!”. Ta ida magansr tare da miƙa hannu da niyar janyo sa. Cikin sauri Ramadan ya sake Matsawa baya tare da riƙe ƙafafun Mommy tare da fashewa da kuka kana cikin raunin murya yace. “Mommy dan Allah kice abarni ni dai yau bana son zuwa makaranta bana so Mommy dan Allah ki barni”. Mommy kuwa Kallonsa tayi lokaci ɗaya taji jikinta yayi masifar sanyi janye ƙafafunta tayi tare da Kallonsa kana tace. “Kai Ramadan wai meyesa bakason zuwa makarantar?”. Cikin kuka sosai yace. “Ayyah Mommy dan Allah yau ɗin nan kaɗai ki barni kada Inje makaranta nafi so yau In wuni ina kallonki kina kallona”. Girgiza kai tayi tare da cewa. “Ramadan kaje yau kaga gobe idan Allah yakai mu Alhamis ne baza kaje makaranta ba zamu wuni agida juma'a ma zamu wuni tare kaga har Asabar ma baza ka jeba”. Girgiza kai yayi still hawaye na bin Fuskarsa yace. “Mommy ni dai bana so”. Miƙewa Khausar tayi tare da kama hannunsa tana jansa shima hannun Mommy ya riƙe yana kuka Khausar na jansa yana jan Mommy da ƙar ta fincike sa suka fita kana ta sanya shi amota tana kallon Haiydar dake hararan Ramadan tace. “Gashi ku tafi”. Kana ta juya ta koma ci. Da yake shi Haiydar haddan safe suke zuwa na maza. Kusa da Mommy ta zauna tare da riƙe mararta tana yarfe hannunta kana ta runtse Idanunta tare da faɗin. “Wayyo Cikina ciwo Mommy!”. Mommy kuwa jikinta ne yayi sanyi kallon Khausar dake riƙe da marar ta tayi tare da cewa. “Ke tashi kijeki ɗauko min Yarona, bana so yau abar minshi kada yaje makarantar nan, tunda tun jiya da daddare yake Matsawa kada abarshi yaje nima raina baya so kawai abarshi ya dawo yafi min tashi ki ɗauko min ɗana”. Ahankali Khausar ta ɗago tare da kallon Mommy kana cikin sanyin murya tace. “Ayyah Mommy cikina ya kama bazan iya ba kuma Mommy meyesa zaki biye mishi?”. Girgiza kai Mommy tayi tare da cewa. “Khausar naji kawai bana so ya tafi ɗauko min shi”. Dai-dai lokacin kuma suka ji Girinirin alamun an rufe gate Kallon Mommy Khausar tayi kana tace. “Toh Mommy kin jin anrufe gate sun tafi”. Ajiyar zuciya Mommy ta sauƙe tare da lumshe Idanunta kana tace. “Toh shikenan Allah ya tsare Allah ya dawo dashi lafiya”. Khausar kuwa Ameen tace tare da kwanciya akan 3sitter still Hannunta na dafe saman maranta. Kallonta Mommy tayi cike da kulawa tace. “Yau kuma cikin ki yau nawa ga wata ne?”. Ahankali Khausar ta buɗe Idanunta tare da cewa. “Yau Sha biyar Mommy”. Jinjina kai Mommy tayi kana tace. “To aima kusan saura kwana huɗuma Period ɗinki yazo date ɗin da saura?”. Kai Khausar ta gyaɗa tare da matsa saman maranta kana tace. “Eh Mommy haka dama yake min kafin kwanakin su cika yana min yawan ciwon ciki”. Numfashi Mommy ta fesar kana tace. “Allah dai ya sawwaƙa kije ki haɗa ruwan zafi da zuma kisha”. Ahankali Khausar ta motsa laɓɓanta tare da faɗin. “Toh”. Kana ta yunƙura zata tashi tayi saurin komawa saboda yanda cikin ya murɗa. Ganin haka yasa Mommy ta miƙe tare da zuba mata Zuma da ruwan zafi akofi ta kawo mata amsa tayi tasha tare da gyara kwanciyar ta akan kujeran tana jin ciwon na sauƙa ahankali Mommy kuwa zaman ta ta gyara akan kujeran tare da lumshe Idanunta... Acan mota kuwa bayan sun isa bakin makarantar Amina dake baya ta kalli Driver tare da cewa. “Malam Habu ka sauƙe su ba sai mun shiga cikin gate ba sai ka wuce ka kaini unguwar Waziri gidansu Samira Sani”. Anutse Malam Habu ya juya ya kalleta kana yace. “In dai shigar dasu kinga Yara ne ba zasu iya tsallaka wa daga kan titin nan ba bare yanda motoci suke wucewa”. Wani kallon ta watsa masa tare da cewa. “Yau suka fara zuwa makarantar kuma ga Haiydar ai zai riƙe su”. Kai Malam Habu ya gyaɗa tare da sauƙe su kana yaja motar ya tafi. Haiydar kuwa juyawa yayi tare da ɗaukar Raudat kana ya juya da nufin zai riƙe hannun Ramadan kawai ya hangosa Atsakiyar titin Aminu kuwa tuni ya tsallaka. Kamar daga sama wata baƙar mota jeep ta taho aguje. Cikin tsananin tashin hankali da ruɗu Haiydar yace. “Innalillahi wa'inna ilahi rajiu'n Ramadannnn”. Motar kuwa da mugun gudu tazo tare da nufar kan Ramadan...! *Littafin SAKAYYAH na kuɗine ƴar uwa ki biya ki karanta cikin Aminci da salama babu haƙƙin kowa a kanki littafin 1k ne 0661110170 GTBank AISHA ALIYU GARKUWA sai ki turo min shaidar biyanki ta WHATSAPP 09097853276* *WOHOHO IN KAJI ANA ƘI GUDU TABBAS SA GUDU NE BEZO BA* _Ina kuke Ma'aurata masu sha'awar ganin sun zama taurari kuma fitilu a idanun mazajensu Uwar gida,Amarya,Tsakar gida,hadda tan kaɗen gida Shararriya kuma ƙasaitacciya data saba kawo muku nau'ikan sirrin sahihan magungunan ma'aurata wato *AYSHA ALIYU GARKUWA* Garkuwar Marubuta ayau ma ta dawo muku da Ingantattun magungunan mata masu kyau da inganci domin gyara kanki ki zamto tauraruwa a idanun mijinki...Muna da Ingantattun Abubuwa kamar haka_ :_Munada Garin mallaka, garin maɗi, garin Hakkin mayi, garin ɓelɗamhi Garin ilanwaddihi, Gumbar da ba'a baiwa mai kishiya, Gumbar kolli mai kellin al'khairi, Gumbar Riɗi wato 3 in 1, Gumbar makwaranyi, Masin Maliƙi mai masifar ƙarfi da matse mace, ka masin Daɗi har Maɗigan Akwai, kwanon ƙasaitacciyar mace mai masifar kyau da ratsa jiki da samar da inƙantacciyar ni'ima yanada abubuwa masu kyau haɗinsa, Zumar goron tula mai masifar kyau, tsumin dabino, mai ratsa jiki, tsumin Riɗi mai ƙarfi, Furar Mata mai tsastsafo da ni'imantaccen damshi, Cida kaza, Ciccibi Abodi, Tsumin Ɓaure, tuwon ɓauren, kana akwai maganin sanyi sadidan, da dai sauransu...Se kuma fannin ƙamshi kasance da Shu'umin ƙamshi wanda ze gigita ƙwaƙwalwar Oga tare da jin ko wacce mace bata kaiba...._ _Shin ko kina da labarin Miskilinci da ƙasaitar Rayyan Naaan amma lokaci ɗaya ya zamto zautacce sakali akan soyayyar Jannart bakomai Jannart ta riƙe ba face sirrinkan gyara da kuma shu'uman humran da kulaccar sirri na Aysha Aliyu Garkuwa(Tubali) tabbas taga tasirin haka domin Naanunta ya zame mata tamkar bawa_ _Shin ko kinsan sihirtaccen haɗin da Aysha ke sha kenan ta zamto tauraruwa a idanun Hamma Yusuf(Miwasmiti)...Tabbas Mahmud ya zamto zautacce kuma makaho akan sauyayyar Bazawara wato khadijarsa duk da kuwa gashi da budurwa(Namiji Baya Kaɗan) ko kinsan hakan nada alaƙa da amfani da sahihan maganin da kuma shu'uman humran Aysha Aliyu Garkuwa??.Nasan ba zaka ku manta da irin kima da kuma darajar da Aysha ke dashi acikin Idanun Sheik Jabeer ɗin ta duk da kuwa shekaru sunja anma jinta yake tamkar budurwa 'yar sha bakwai(Garkuwa) sirrin hakan na tare da Ingantattun kuma sahihan magungunan Aysha Aliyu Garkuwa Wato Garkuwar Marubuta da kuma Ma'aurata na tabbata kunsan da cewa basirarta ba'a iya rubutun littafi ya tsaya ba hadda inganta rayuwar ma'aurata ta hanyar kawo musu Nagartattun abubuwa Ga duk wacce ta shirya saya seta tuntuɓi number ta 09097853276 muna iya tura kayan mu aduk inda kuke afaɗin Nigeria harma da ƙetare Dan Allah 'yar uwa idan baki shirya siyaba kada kiyi min magana muɓatawa kanmu lokaci...._ 🤝🏻🤝🏻🤝🏻🤝🏻🥰😘sai.kunzo. sayan na gari maida kuɗi gida, *By* *GARKUWAN MARUBUTA* [30/07, 1:40 PM] Halimatu A/rahman Sadeeya: *GARKUWAR* taku ce dai MA'AURATA, da masu shirin aure, da masu jego, da yan gayu masu son k’amshi kece raini, da gyaran da zaike maimaita muku dararen forkon kuruciya* Ko kunsan Jikinmu na da sinadaran hormones da suke taimakawa dan’adam akan komai musamman lokacin da mace take mu’amalar aure da mijinta. Mafi akasari wannan hormones din ne ke samun matsala ko su yi sanyi koma su daina aiki kwata-kwata shi ne dalilin da zai sa mace tace bata jin sha’awa ko bata san dadin aure ba. Albishirinku ina da kayan da ke taimakawa wannan sinadaran du dawo aiki tukuru don karkato miki da kimarki wajan mai gida sannan su taimakawa wannan sinadaran hormones dinki su dinka secreting din ni’ima wadatacciya da zata taimaka miki ki gamsu mijinki ya gamsu fiye da tunaninki. Note: Kayana ba sa tsinka ruwan ni’ima suna dai taimakawa hormones dinki ne su tsattsafo da ni’imar musamman wacca cutar sanyi ko dattin mahaifa ya dankarar da su ya hana su yin aikinsu yanda ya kamata. Haka zalika idan kina da kyau ki kara da wanka. Zaki iya amfani da magani na na gargajiya wanda zai gyara miki sex hormones din kullum ki kasance cikin humidify wato cikin damshi mai albarka kamar yanda ake son mace. Yana gyara miki mara. Sai kamshi. Hajiyata daure ki fara amfani da turarena ki ji irin salon kamshin sa salo ne da zai daidaita ki da mijinki ya kankaro miki da kimarki a wajansa. Siyan na gari mayar da kudi gida. Ga masu buƙata ga number' wayata wanda nake whatsApp dashi 09097853276 kimin mgn ta whatsApp in har kin tabbatar kin shirya saya mu dai-dai ta, kayana ba ƙanana bane, shiyasa bana harkan karanta, muddin kinsan baki shirya sayaba Please kada kiyi min mgn ki bari sai kin shirya kuɗinki a hannu, ba ina nufin kayana bana talaka bane, no akwai ƙananan set na masu karamin karfi, banson aimin mgn a ɓatamin lokacin aiyukana a shirme baki shiryaba. Shine karantan da bana so. 0005388578 Jaiz bank AISHA GARKUWA ALIYU. In kin shirya ga number ta ga kuma account number ta wanda in mun gama mgn zaki turo kudin ki, kana insa miki kaya a mota, duk ƙasar da kike kayana zaije gareki, amman fa in kinada dalilin zuwan nasune🤝🏻sayan na gari meda kudi gida. GARKUWAR MA'AURATA *Littafin SAKAYYAH na kuɗine ƴar uwa ki biya ki karanta, cikin Aminci domin ko kin gashi a wasu wuraren toh na satane na Allah ya isane, Yaseen kuwa wlh na Allah ya isan ne duk ƙanƙatar haƙƙina ban yafeba, yake yar uwa mai tsoron Allah da kikaye haƙin wani ki biya 1k ne kacal 0661110170 GTBank AISHA ALIYU GARKUWA sai ki turo min shaidar biyanki ta WHATSAPP 09097853276, sai in saki a Group ɗin, ku kuma masu fitar da littafina ki da Allah, Allahu Rabbi ya isarmin wahalata da nasha kusan tsawon shekara ina rubutu. Dan ki biya 1k kudin karatu kike fitarwa mutun sama da ɗari, toh yadda kika tozarta min kasuwanci ne kema Allah ya haɗaki da mai miki fiye da abinda kikayi min, kuma ki sani wlh ban yafeba* Isrnett. Gaban motar ne ya bugi Ramadan, kamar gilmawar walƙiya ya faɗi agefen kwaltan. Akuma dai-dai lokacin motar Moddibo da M Jameel ya tsaya awajen cikin sauri M Jameel ya buɗe motar tare da fita yana cewa. “Innalillahi wa'inna ilahi rajiu'n”. kana ya nufi inda Ramadan ke kwance. Moddibo kuwa kansa ya dafe tare da rintse idanunsa. Akuma dai-dai lokacin Malam Isa,Malam Ahmad da malam Sa'id suka ƙara so Kasancewar lokacin ne Malamai suka fara zuwa wasu ma ko Parking basuyi ba. Motar daya bige Ramadan kuwa ko tsayawa bai yiba ya ɗiba aguje. Aminu kuwa cikin tsoro da tashin hankali ya juya tare da kallon Ramadan dake kwance yayin da M Jameel ke tsugunne kansa zuwa lokacin tuni Ramadan ya suma ɗagosa M Jameel yayi tare da ɗan buga kuncinsa yana cewa. “Ramadan! Ramadan!!”. Amma ko motsa wa baiyi ba alamar babu nunfashi atare dashi. Cikin sauri Malam Arɗo ya fito daga cikin makaranta kasancewar ɗaya daga cikin Malaman yashiga ya sanar masa an samu hatsari awaje. Moddibo kuwa cikin sauri yayi wa motar key tare da ƙoƙarin bin bayansu ganin basu da niyyar tsayawa yana ƙoƙarin gilmawa M Jameel ya ɗaga masa hannu tare da faɗin. “A.J ka tsaya mu ɗauke sa mu kaisa asibiti”. Jin haka yasa Moddibo fasa bin bayan motar kana ya tsirawa bayan motar Ido ya tsaida ganinsa kan number burki ya taka. M Jameel kuwa cikin sauri ya ɗauko Ramadan ya sanya shi cikin motar ya tada suka nufi asibiti, Malam Arɗo kuma motar Malam Isa suka shiga tare da kallon sauran Malaman dake tsaye kana yace. “Malam Isma'il ku shiga ciki”. Kana Malam Isa yaja motar suka tafi. Haiydar kuwa har zuwa yanzu ya kasa buɗe Idanunsa saboda tsananin tsoro da tashin hankali ji yake yana buɗe idanunsa zai ga ƙwaƙwalwar Ramadan abaje akan kwalta hakan yasa ya runtse Idanunsa kana ya sanya hannunsa duka biyu ya dafe kansa yayin da gaba ɗaya ilahirin jikinsa ke rawa. Raudat kuwa kuka take tamkar ranta zai fita yayin da take yarfe hannunta tare da bubbuga ƙafarta tana cewa. “Wayyo Ramadan ina za ku kaisa Meyesa mesa Wayyo Ramadan ɗina!”. Malam Isma'il ne ya ƙara so kusa da Haiydar tare da riƙe hannunsa ganin yanda jikinsa ke rawa kana yace. “Haiydar buɗe idon ka”. Girgiza kai Haiydar yayi still cikin Muryan kuka yace. “A'a tsoro nakeji in buɗe ido na inga ƙwaƙwalwan Ramadan akan kwalta”. Girgiza kai Malam Isma'il yayi tare da cewa. “Babu komai babu abinda ya sameshi beji ciwo ba motar ce ta bigesa ya koma gefe amma bata bi ta kansa ba!”. A hankali ya buɗe Idanunsa da sauri kuma ya sake ware su ganin babu kowa sannan Ramadan ma baya nan cikin rawan murya ya kalli malam Isma'il tare da cewa. “Ina Ramadan ɗin?”. Kallon titin Malam Isma'il yayi tare da faɗin. “Malam Jameel da Moddibo sun tafi kaishi asibiti sannan Malam Arɗo yabi bayansu yanzu kutafi cikin makaranta ka kwantar da hankalinka kaji?”. Girgiza kai Haiydar yayi yace. “Ya za'ayi kace in kwantar da hankalina kansa yafashe ko? ya karye ko? Ko dai ya mutu ne?. Cikin sa ya fashe ko? Kan kare sa akayi akwalta ko!?”. Duk alokaci ɗaya ya jero masa tambayar. Girgiza kai Malam Isma'il yayi kana yace. “Wallahi babu abinda ya sameshi kawai dai tsoro ne idan mutum bai taɓa accident ba dole tsoro zai sa ya suma kaje kashiga cikin makarantar maza kushiga ciki”. Dai-dai lokacin kuma ɗalibai suka fara zuwa cikin rarrashi Malam Isma'il yace. “Ku shiga ciki”. Raudat kuwa kuka ta riƙa yi tana yarfe hannu tsugunna wa Malam Isma'il yayi ya ɗauketa suka shiga cikin makarantar kana ya shiga bawa Haiydar ƙarfin guiwa. Acan ɓangaren su M Jameel kuwa suna isa Hospital ɗin aka karɓi Ramadan tare da kaisa Emergency Room. Atake aka fara bashi temakon Gaggawa kasancewar akwai ƙwararrun Likitoci cikin ikon Allah beji wani rauni ba sai karaya daya samu aƙafarsa na hagu. Cikin mintunan da baza su gaza talatin ba ya farfaɗo tare da fashewa da kuka kana ya buɗe Idanunsa tare da cewa. “Wayyo ƙafata Addah Khausi Ƙafata, Wayyo Addah Khausi Ƙafata”. Ahankali Moddibo dake gefensa ya matsa tare da riƙe hannunsa kana yace. “Sorry Ramadan kayi haƙuri kayi shiru kaji”. Cikin kuka sosai Ramadan ya kallesa tare da cewa. “Mommy na Malam akaini wajen Addah Khausi. Ina Addah Khausi na Ƙafata ciwo yake min zafi?”. Ya ida maganar yana jujjuya kai yayin da gaba ɗaya zufa ya wanke masa ilahirin jikinsa Musamman saman goshin sa amma babu hawaye a Idanunsa yayinda ƙafansa ya sake kamar roba ya langwaɓe. Cike da rarrashi da kuma tausayawa Moddibo yace. “Kayi haƙuri zai daina insha Allah”. M Jameel kuwa magunguna da abubuwan da za'ayi ɗauri Dr ya rubuta masa kana ya ya fice tsaye ya samu malam Arɗo maƙale da waya akunnen da alama da Lamiɗo yake magana. Cikin yanayin jimami ya gyara zaman wayar akunnensa tare da cewa. “Wallahi kuwa akwai yaron wajenka da mota ta ɗan kuskuresa yanzu haka ma muna asibiti”. M Jameel ne ya gyara tsayuwar sa tare da harɗe hannunsa aƙirji kana ya lumshe idanunsa. Cikin sauri Malam Arɗo yace. “A'a ka kwantar da hankalin ka Mai Martaba baiji wani ciwo ba. Dan Allah dan Annabi ka kwantar da hankalin ka”. Ganin Malam Arɗo ya katse kiran yasa M Jameel cewa. “Malam wai batun ɗauri ne ƙafarsa ta karye to yanzu ance za'a yi masa ɗauri”. Jinjina kai Malam Arɗo yayi kana suka fita da M Jameel. A can Gidan Lamiɗo kuwa tun bayan tafiyarsu Ramadan Makaranta Mommy ta kasa miƙewa taje ta gyara ɗakin mijin nata. Duk da kuwa cewa itace da girki baki ɗaya jikinta Asanyaye yake bata da wani kuzarin kirki yayin da Khausar ke kwance gefenta har zuwa lokacin hannunta na dafe da maranta. Ajiyar zuciya Mommy ta sauƙe tare da furzar da iska mai zafi daga bakinta kana ta yunƙura da niyyar miƙewa dai-dai lokacin Lamiɗo ya shigo bakinsa ɗauke da sallama. Yana shiga idanunsa akan Mommy tare da cewa. “Aysha!, Aysha”. Cikin sanyin murya da mutuwar jiki Mommy tace. “Na'am”. Sai da yayi ƙoƙarin dai-dai-ta nutsuwarsa tare da cewa. “Zo muje ki rakani?”. Kallon Mamaki Mommy tayi masa tare da faɗin. “Ina zamu je?”. ƙasa yayi da kansa kana yace. “Ke kam zoki rakani wani waje mana”. Atake zuciyarta ya tsinke ƙirjinta ya buga da masifar ƙarfi kana tace. “Rakiya kuma ina kuma zamuje. Mai Martaba ka faɗa min?”. Ta ƙara sa maganar tare da kallon ƙwayar idanunsa da take iya hango tsantsar tashin hankali da damuwa. Cikin rawan murya tace. “Meyesa mu Ramadan”. Jin abinda tace yasa Khausar dake kwance tayi saurin miƙewa Atake Idanunta suka cika da ruwan hawaye lokaci ɗaya tsoro ya rufeta!. Cikin dakiya Lamiɗo yace. “Babu Abinda Ya samu Ramadan ke kam zoki rakani”. Cikin yanayin sadaukar wa Mommy ta kallesa kana tace. “Dan Allah ka faɗa min Meya samu Ramadan ɗina!”. Ajiyar zuciya ya sauƙe tare da cewa. “Kizo mu tafi mana”. Miƙewa Khausar tayi cikin rawan murya dan tuni hawaye suka wanke mata fuska kana tace. “Dan Allah Abba inzo mu tafi”. Kai ya gyaɗa mata tare da cewa. “Eh”. Cikin sauri ta sanya dogon hijabinta dake fitar da sanyayyan ƙamshin ta fita, shima Lamiɗo fita yayi sashen Hajiya Bunayya ya nufa yana kirata kasancewar shi kansa be san waya samu hatsari acikin ƴaƴan nasa ba Haiydar, Aminu, ko Ramadan. Mota suka shiga Khausar na gaba Lamiɗo Gimbiya Bunayya da Mommy suna baya. Lokaci ɗaya hankalin Mommy ya sake tashi ganin sun nufi hanyar asibiti cikin tsanananin tashin hankali tace. “Innalillahi wa'inna ilahi rajiu'n dan Allah Mai Martaba ka faɗa min me yasamu Ramadan ɗina?”. Girgiza kai yayi tare da kallonta kana yace. “Nima kaina ban sani ba Aysha babu yanda muka iya da hukuncin Ubangiji”. Hajiya Bunayya kuwa ƙasa tayi da kanta cikin tsananin farin ciki da jin daɗi ta saki murmushi aranta tace Alhamdulillah burina ya cika in. Allah ya yarda yau ankawar min da Haiydar da Ramadan na huta dole inƙara musu kuɗi me tsoka yanda zasuji farin ciki na kawar min da ƴaƴa biyu maza ɗin nan shikenan Mai martaba bashida wani ɗa Namiji sai Aminu dole Aminuna shi zai gaji sarauta. Ahankali ta ɗago kanta Idanunta cike taf da ruwan hawaye ta kalli Lamiɗo tare da cewa. “Innalillahi Wa'inna ilahi rajiu'n. Mai martaba mai yafaru?”. Cikin yanayin damuwa yace. “Ni kaina ban sani ba ance min dai ɗana Namiji ne amma ban sani ba Aminu ne...”. Aruɗe Hajiya Bunayya tasa hannu ta dafe ƙirjinta tare da cewa. “Innalillahi wa'inna ilahi rajiu'n ɗaya-ɗayan nawa”. A hankali ya fesar da iska daga bakinsa kana yace. “Kuma ban sani ba ko Haiydar, ko Ramadan ne ban sani ba sai mun shiga”. Mommy kuwa lumshe Idanunta tayi tare da faɗin. _“Innalillahi wa'inna ilahi rajiu'n Allahumma Ajirni fii musibati wa'ahlifli khairan min ha”_. Suna isa suka fito bayan Driver Yayi parking Malam Arɗo na ganin Lamiɗo yayi saurin miƙewa tare da isa inda suke kana yace. “Sannunku da zuwa Mai Martaba”. Khausar kuwa tun da suka fito take kuka baki ɗaya jikinta ya gama bata Ramadan ne kuma ya rasune. Batare da Lamiɗo ya amsa Barka da zuwan da yake masa ba yace. “Acikin ƴaƴana waye ne yasamu hatsarin?”. Malam Arɗo ya gyara tsayuwar sa tare da cewa. “Ƙaramin ne”. Ƙasa daure wa Khausar tayi kuka ta fashe dashi tare da faɗin. “Innalillahi wa'inna ilahi rajiu'n Mommy Ramadan ne, sai da yace kada yaje makaranta yau kawai abarshi kada yaje kamar yasan me zai faru dashi na nace dole na muka turashi”. Mommy kuwa kasa daure wa tayi hawaye masu zafi suka shiga zubo mata. Dai dai lokacin M Jameel ya dawo daga sayo magungunan a Pharmacy dake cikin Hospital ɗin. Kallon Malam Arɗo Lamiɗo yayi kana yace. “Ku kaimu ciki”. Kai M Jameel ya gyaɗa tare dayi musu Jagora kasancewar Mai matarba ne da iyalansa yasa aka barsu suka shiga. Suna Shiga idanun Khausar ya sauƙa akan Moddibo dake Rungumeta da Ramadan yana lallashinsa. Ramadan na kallonta ya fashe da sabon kuka tare da cewa. “Adda Khausi ƙafata Addah Khausi zoki riƙe min ƙafata”. Kallonsa ya mayar kan Mommy tare da cewa. “Mommy ancire min ƙafata ko? Bana jinta a jikina”. Sai kuma ya kalli Lamiɗo daya zuba masa Idanu cikin matsanancin kuka yace. “Abbah Ƙafata, Ƙafata”. Kallonsa ya mayar kan Hajiya Bunayya ya langwaɓar da kai amma baice komai ba. Hajiya Bunayya kuwa kallon Moddibo tayi jikinta na tsuma tace. “Ina Haiydar kadde shi yana mutuware?, Innalillahi wa'inna ilahi rajiu'n”. Ido Moddibo ya zuba mata tare da tsaida idanunsa acikin nata abinda ba ɗabi'arsa bace ba kuma al'adarsa bace haɗa ido da mutum amma haka nan ya tsinci kansa da tsaida idanunsa akan matar yana kuma nazartan ta. Cikin yanayin ɓacin rai M Jameel ya juya ya kalleta tare da cewa. “Haba Hajiya wannan wani irin kalma ne ya za ayi kice yana mutuware?”. Hannu tasa tare da share hawayen fuskarta kana tace. “To ina yake? Ina Haiydar Allah sarki babban ɗan mu wanda zai gaji Mahaifinsa a sarauta Wayyo Haiydar”. Malam Arɗo da shigowarsa kenan ya kalleta tare da cewa. “Haiydar na nan lafiya yana makaranta yana karatu kana suna cikin kulawa!”. Da sauri Ta haɗiye wani abu mai masifar ɗaci tare da cewa. “Toh Ina Aminuna?”. Cike da kulawa malam Arɗo yace. “Shima yana cikin ƙoshin lafiya wannan ne kaɗai Accident ɗin ya faru dashi”. Lokaci ɗaya wani masifaffen ɓacin rai da baƙin ciki ya mamaye zuciyarta cikin ranta tace Haiydar bai mutu ba sannan shima wannan karayane ka ɗai?”. Tsaban zancen zuci dake cinta saida kalmar Karaye ne kaɗai ya fito fili. Atare Khausar da Moddibo suka kalleta jin abinda tace wannan ɗin ma Karaye ne kaɗai Moddibo ya maimaita kalmar Aransa. Khausar kuwa kwallon ta tayi tare da tsareta da ido tana sake maimaita kalmar aranta. Malam Arɗo ya kalli Lamiɗo tare da cewa. “Mai Martaba karaya yasamu dama akan za'a yi masa ɗauri ne saboda Andu basa gaba ɗaya baiji wani ciwo ba Karayane da Allah ya ƙadarta toh insha Allah yanzu za'a yi masa ɗauri”. Jinjina Kai Lamiɗo yayi tare da cewa. “Mun gode Allah ya saka da alkhairi”. Cike da damuwa Malam Arɗo yace. “Dan Allah kayi haƙuri akasani ne, tsautsayi aka samu wanda baya wuce ranan sa mai motar kamar da gayya yayi ko tsayawa bai yiba ya gudu baki ɗaya abin yazo da akasani ne bamu taɓa samun irin wannan akasin abakin makarantar ba”. Girgiza kai Lamiɗo yayi tare da cewa. “Bakomai Malam Arɗo ai babu yanda muka iya da ƙaddara ko agadon Mahaifiyarsa yake idan Allah ya ƙadarta zai karye dole ya karye Waman Ƙadarallahu Haƙƙa ƙadrihi”. Kai Malam Arɗo ya gyaɗa tare da cewa. “Haka ne kam”. Ajiyar zuciya Lamiɗo ya sauƙe tare da faɗin. “Amma bana son ɗaurin asibiti zamu koma dashi gida ayi masa na Gargajiya”. Jingina kai Malam Arɗo yayi tare da cewa. “Toh shikenan Babu matsala”. M Jameel ya Kalli Ramadan cike da tausayawa kana yace. “Toh Mai Martaba Allah ya ƙara sauƙi”. Kana ya miƙa masa ledan maganin daya sayo yace. “Gashi magunguna ne na rage zugi da zafin ciwo koda ɗaurin gidan za'ayi masa za ayi amfani dasu”. Karɓa Lamiɗo yayi tare da faɗin. “Toh angode”. Kana ya sanya hannu acikin aljihu ya ciro wayarsa tare da kiran number Malam Bala mai ɗauri. Katse wayar yayi bayan sun gama mga, juyawa yayi ya kalli Hajiya Bunayya da Mommy kana yace. “Mutafi to”. Sai kuma ya juya ya kalli Khausar dake kuka hadda sheshsheƙa yace. “Haba Addah Khausi kiyi haƙuri mana ai sai ki ƙara tayar masa da hankali shi yana kuka yana kiran ki sannan kema kina kuka ki bashi ƙarfin gwiwa mana”. Kai ta gyaɗa tare da Matsawa kusa dashi still Moddibo na riƙe dashi bakin gadon ta ƙara sa Moddibo kuwa saurin lumshe idanunsa yayi. Ita ko Khausar cikin kuka ta kalli Ramadan tare da cewa. “Kayi haƙuri Ramadan da mun sani da baka je makarantar nan ba tun jiya kake cewa baza kaje ba kana ta roƙon Mommy kada kaje”. Kallonta ta mayar kan Mommy tare da faɗin. “Dan Allah Mommy duk sanda yaron nan ya sake cewa ba zaije makaranta ba kada abarshi yaje tun jiya yake ta roƙo yau ɗaya abarshi ya huta kamar yasan abinda zai faru dashi”. Kasa cewa komai Mommy tayi ɗan ita kaɗai tasan yanda zuciyar ta ke mata. Khausar kuwa ahankali ta tsugunna akan Ramadan ganin yanda goshinsa ke tsats-tsafo da zufa ta ɗago lallausan tafin hannunta tare da mannawa agoshin sa ta yarfe masa zufan. Ahankali Moddibo ya tsirawa tafin hannunta Idanu cikin wani irin yanayi sannu Ahankali tsikar jikinsa ya fara tashi lumshe idanunsa yayi kana ya tuna lokacin da Amafarki ta sanya Lallausan tafin hannunta tana shafa Sajensa, ɗan juya hannunta ya buɗe Idanunsa da suka sauya launi tare da kallon hannunta yanda take shafa goshin Ramadan ɗin cikin nutsuwa yasa yaji wani abu mai masifar ƙarfi ya tsirga masa tun daga kan yatsan ƙafansa har zuwa ƙwaƙwalwar kansa lokaci ɗaya... ɗin sa ya harba da ƙarfin gaske cikin sauri ya cije lips ɗin sa tare da lumshe idanunsa yana kiran Sunan Allah Aransa. M Jameel ya juya ya Kalli Moddibo da Idanunsa ke lumshe kana yace. “Mu tafi ko?”. Kai ya gyaɗa tare da yunƙurawa ya ɗauki Ramadan dake ta faman kuka Khausar ta kauce gefe tana sakin ajiyar zuciya. Anutse Moddibo ya juya ya fita kana suma suka fice daga ɗakin zuwa harabar asibitin yana isa jikin motar ya samu har Lamiɗo yashiga gaba kana Mommy tashiga baya cikin sauri Hajiya Bunayya tace. “Kawo shi nan in riƙe shi”. Banza Moddibo yayi tamkar baiji me tace ba haka nan zuciyarsa ke raya masa Mommy ce mahaifiyarsu saboda kammani kana ga yanda Khausar ke kiran sunan Mommy akai-akai haka ma Ramadan yasa ya fahimci itace Mahaifiyarsu. Buɗe bayan motar yayi tare da kallon Mommy da hankalinta ke tashe ahankali ya ɗago Ramadan tare da ɗaura mata shi akan cinyarta. Cikin sanyayyar muryarsa mai cike da kamala nutsuwa da ladabi da kuma ƙwarjini yace. “Mommy dan Allah kada ki tada hankalin ki. Insha Allah zai samu lafiya ki cigaba dayi masa addu'a”. Jinjina kai tayi tare da cewa. “Nagode Allah ya saka maka da alkhairi Ubangiji ya Albarkanci rayuwar ka nagode”. Kansa a ƙasa ya amsa da. “Ameen Allah ya sawwaƙa”. Sannan ya rufe musu mota. Driver yaja suka tafi kana Moddibo da M Jameel suka shiga motarsu suka tafi. Sannan Malam Arɗo da Malam Isa suka shiga mota suka tafi. Ahankali Moddibo ke Driving yayin daya tsirawa titin Idanu,M Jameel dake gefe ya sauƙe ajiyar zuciya tare da cewa. “Kai Allah ya gyara wannan al'amarin Ubangiji Allah ya ƙara tsarewa ya kare gaba!”. Anutse M Jameel ya juya ya kalli Moddibo jin bai amsa addu'ar tasa ba cike da kulawa yace. “Ya dai? A.J meyafaru ne kayi shiru? Ina ta magana ba reply?”. Ajiyar zuciya Moddibo ya sauƙe tare da furzar da iska mai zafi da kallon M Jameel kamar wanda aka fisgo maganar daga bakinsa yace. “Wannan Accident ɗin shiryeyyene!”. Zare ido M Jameel Yayi tare da cewa. “Kamar ya shiryeyyene?”. Ƙaramin tsaki Moddibo yaja kana yace. “Akwai abinda ban gamsu dashi ba amma babu komai insha Allah zamuyi bin cike saboda na ɗauki number Motar Allah dai yabawa yaron nan Lafiya”. Sauƙe numfashi yayi tare da fesar da iska daga bakinsa kana yace. “Kaga yanda mahaifiyarsa tashiga tashin hankali amma matar nan da suka zo da ita hmmmm”. Sai kuma yayi shiru tare da faɗin. _“Astagfirullah Wa'atubu Ilaik ³_”. A hankali ya numfasa tare da cewa. _“Azzanna zambu walau kana haƙƙun,_ Allah kagafar ta min Allah kaya femin munana zato dana yi mata”. Kallon M Jameel Yayi kana yace. “J bangamsu da yanayinta ba”. Jinjina kai M Jameel yayi tare da cewa. “Sosai ma nima na lura da wani yanayi atare da ita amma dai Astagfirullah Allah mun tuba”. Har suka shiga makarantar ba wanda ya sake magana Moddibo na Parking ya fita. Acan gidan Lamiɗo kuwa bayan sun isa Lamiɗo ya riko Ramadan aka kafadarsa Already mai ɗaurin yazo kai tsaye sashen sa ya nufa dashi cikin sauri Mommy ta tsaya daga gefensa cikin raunin murya tace. “Mai Martaba akaishi wurina kawai aje amasa acan”. Kallon ta Lamiɗo yayi kana yace. “Aysha aje amasa awaje na kawai ni yakamata inyi jinyarsa tunda yaro na miji ne”. Girgiza kai tayi kana cikin sanyin murya tace. “Zaka bar uzurorin kane ai ƙaramine zan iya yi masa komai yanzu da Haiydar ne zaka iya cewa zai fi ƙarfin indinga ɗaga sa ko kuma yi masa wani abu”. ta faɗa Idanunta na zubar da hawaye Jinjina kai Lamiɗo yayi tare da cewa. “In dai har kina so in Samu ƙarfin gwiwa kidena zubar da hawaye kin san Banason ganin hawayen ki”. Khausar kuwa tuni ta bar wajen. Bayan sun shiga falon Mommy Malam Bala ya ɗaura ƙafar cikin tsanananin azaba Ramadan ke kuka saboda zafi da raɗaɗi daya ke ji miƙewa Mommy tayi tashiga Bedroom ɗin tana hawaye cike da tausayinsa Khausar ma miƙewa tayi ta shige Bedroom ɗin ta yana sheshsheƙa ba zata iya juran Kallonsa cikin ciwo ba Lamiɗo kuwa riƙe sa yana rarrashin sa bayan angama ɗaurin Malam Bala ya basu magunguna da za'a shafa ledan da M Jameel ya bashi ya ɗauko tare da ɓalla masa maganin ya bashi sannun ahankali Ramadan ya fara sakin Ajiyar zuciya nan da nan bacci ya ɗauke sa miƙewa Lamiɗo yayi ya kwantar dashi akan 3sitter kana ya nufi Bedroom ɗin Mommy. Hajiya Bunayya kuwa ganin ba kowa afalo yasa ta sanya hannunta abakin zaninta tare da ciro wayarta kana tayi dearling wani Number tana Jin anyi picking tayi ƙasa da murya tare da cewa. “Ya haka? Shima wanda kuka buge ɗin karaya ne fa kaɗai!?”. A kuma dai-dai lokacin Khausar ta fito daga Bedroom ɗin ta jin falon yayi shiru ta ɗago manyan Idanunta da sukayi ja ta kelleta. Cikin basarwa Hajiya Bunayya tace. “Wallahi Allah ya taƙaita karaya ce kaɗai toh Nagode”. sannan ta katse wayar. Jinjina kai Khausar tayi tare da Kallon ta babu walwala atare da ita tace. “Hmmm Mai rabon ganin baɗi dai zai gani koda ana kamawa ana sawa aturmi ana kirɓawa, kana zakaran da Allah ya nufa da cara ko ana ga muzuru ga shaho sai yayi”. Hararan ta Hajiya Bunayya tayi tare da cewa. “Ni tsiyata dake kin cika habaici da zaurance gaki Bafulatana amma kamar ba haushiya”. A kuma dai-dai lokacin Mommy da Lamiɗo suka fito daga Bedroom ɗin suna murmushi Mommy na Kallon Hajiya Bunayya tace. “Yaya keda Khausar dai”. Murmushin yaƙe Hajiya Bunayya tayi tare da cewa. “Ai lallai dai kam”. Kallon Lamiɗo Mommy tayi kana tace. “Yayi bacci”. Jinjina kai yayi tare da cewa. “Eh kafin ya tashi ya kamata adafa masa kaji ahaɗa da maganin da Bala ya bada yana tashi sai abashi yaci”. Kai Mommy ta gyaɗa tare da karɓa, Khausar ta kalli Mommy tare da faɗin. “Mommy kawo inje in dafa masa ainaga kamar akwai sauran kaji a fridge kana ta wuce kichen ɗin”, Jinjina kai Mommy tayi tare da miƙa mata. Acan Makaranta kuwa Haiydar na ganin Moddibo da M Jameel sun shigo ya miƙe da sauri tare da riƙe hannun Raudat da har zuwa lokacin take kuka kana ya nufi wajensu. Cikin sanyun muryan yace. “Malam ya jikin Ramadan?”. Cike da kulawa Moddibo ya kallesa cike da tausayi ya riƙe hannun Haiydar acikin nasa tare da cewa. “Bakomai fa ya samu lafiya karaya ne kaɗai Abbanku yaje ya ɗauke sa ankoma dashi gida za ayi masa ɗaurin gida ka kwantar da hankalin ka Haiydar ba komai insha Allah”. M Jameel kuwa Raudat ya ɗauka tare da kallon Moddibo kana yace. “Ita wannan kam Malaman su sunce ba tayi karatu ba sai kuka”. Ahankali Moddibo ya juya ya kalleta baki ɗaya fuskarta yayi ja Idanunta sun kumbura kana jikinta ya ɗauki zafi cikin sanyin murya yace. “Kiyi haƙuri Hassan ɗinki yana lafiya babu abinda ya sameshi zaki koma ki same shi agida cikin ƙoshin lafiya Insha Allah”. Kallonsa tayi tare da cewa. “Da gaske!?”. Kai ya gyaɗa mata. “Toh zamu koma gida yanzu”. Ta faɗa tare da fashewa da kuma hadda sheshsheƙa. Ajiyar zuciya M Jameel ya sauƙe tare da kallon Moddibo kana yace. “Ina ganin ya kamata abarsu su koma gida dan yau ɗin nan ko sun zauna bawani karatu zasuyi ba ga Haiydar dake Babba ma baki ɗaya agigice yake bare ita yarinyar sai kuka take duk jikinta yayi zafi”. Jinjina kai Moddibo yayi idanunsa akan Raudat yace. “Eh hakan yayi sai su koma gida kawai”. M Jameel na Kallon Haiydar yace. “Bari akira gida sai aturo Driver yazo ya ɗauke ku”. Kai Haiydar ya gyaɗa kana ya nufi Office ɗin Malam Arɗo ya sanar masa nan Malam Arɗo ya kira Lamiɗo babu daɗewa Driver yazo ya ɗauke su. Suna isa gida Raudat ta fice da gudu tare da shiga falon Idanunta ya saƙa akan Khausar dake zaune gefen Ramadan tana bashi kazar da already ta gama dafawa shi kuwa yana amsa yana ci Zugin ƙafar yayi sauƙi Sosai sai abinda ba arasa ba da gudu Raudat ta shiga tare da ƙara sawa ta rungume kan Ramadan cikin sauri ya ɗaga mata hannunsa na hagu tare da nuna mata ƙafar sake sa tayi tare da komawa gefensa ta zauna kana tace. “Ya ƙafan ka?”. Murmushi yayi tare da cewa. “Da sauƙi”, Langwaɓar da kai tayi kana tace. “Allah ya ƙara sauƙi sannu³”. Haiydar kuwa zama yayi agefensa tare da rintse idanunsa hawaye masu zafi suka zubo masa ahankali ya buɗe Idanunsa tare da sauƙe su akan Mommy kana yace. “Mommy tamkar gimmawar walƙiya haka naga motar nan tazo ta bugi Ramadan sanda yayi sama kafin ya faɗo Mommy banyi tsammanin kansa ba zai fashe ba”. Khausar dake cirewa Ramadan ƙasusuwa ajikin kazar ta ɗago kanta tare da miƙawa Ramadan tsokar kana ta mayar da kallon ta kan Haiydar tace. “Allah ne ya kare Haiydar saboda addu'ar mahaifiyarmu saboda haka Ubangiji zai ci gaba da kare mu yana mana katangar ƙarfe da magauta!”. Da sauri Mommy dake cirewa Raudat Uniform ta ɗago ta kalleta kana tace. “Khausar wasu magautan kuma wannan ai ƙaddara ce wacce ta riga fata”. Murmushi mai ciwo Khausar tayi kana tace. “Hmmm Mommy kenan”. Acan ɓangaren Hajiya Bunayya kuwa bayan tashiga ɗaki zaune ta samu Amina hannunta riƙe da Tuffa tana ci, Amina na kallonta tace. “Mommy ba abinda ya sameshi ko?”. Ƙwaffa Hajiya Bunayya tayi tare da zama kana cike da takaici tace. “Ai shi Haiydar ba abinda ya sameshi ko ƙwarzani bai yiba. Ramadan ne kaɗai ya bugu ba wani na arziƙi ba Karayane kaɗai”. A kufule ta ajiye Mayafinta tare da kallon Amina data tsareta da ido kana tace. “Na kirasu munyi magana dasu sannan na nuna musu ɓacin raina sai suka ce wai abinda yasa haka saboda lokacin Malamai sun fara zuwa idan suka tsaya za'a iya kama su”. Ya mutse fuska Amina tayi kana tace. “Ai dai kam sai ahankali”. Hannu tasa tare da ɗaukar Ayaba a Plate dake gaban Amina kana tace. “Ɗazu bayan kin dawo ina kika tsaya dana shigo ban ganki bane?”. Murmushi Amina tayi tare da cewa. “Ina side ɗin Gimbiya Dadu nida Uncle Naseer”. Wara Ido tayi kana tace. “Allah ko?,Ni dai Amina da zaki yarda sannan badan Masifar Son da yake yiwa wannan shegiyar Khausar mai kama da sadaka Yallanba yanda yaron nan ya samu cigaba da arziƙi ga kuma arziƙin da Iyayensa suke dashi da kin haƙura da Jameel din Nan duk da kuwa arziƙin da Mahaifin sa yake dashi”. Ƙwaffa Amina tayi tare da cewa. “Nifa Mommy Ina son Uncle Naseer kuma Ina son Malam Jameel saboda gaba ɗayan su suna da kuɗi kuma dama Ni ko Malam Jameel saboda kuɗin sa nake son sa”. Sai kuma tayi saurin cewa. “Yawwa Ummah ni kuwa Akwai Aure atsakanin mu Uncle Naseer?”. Jinjina kai Hajiya Bunayya tayi tare da ajiye ɓawon Ayaba kana tace. “Sosai ma kuwa Akwai Aure atsakanin ku ko a musulunci ya halatta”. Kai Amina ta gyaɗa tare da faɗin. “Ummah kiga yanda yake kashewa yarinyar nan kuɗi kinga wayar daya siya mata kuwa wayar kusan dubu ɗari huɗu da hamsin kinga siye-siye tunda kinga Malam Jameel Anyi anyi aka mashi awajen Boka an kasa tunda shi wannan yana da riƙo da Ibada shi kuma wannan shgirigirbaune za'ayi saurin kamashi”. Jinjina kai Hajiya Bunayya tayi tare da cewa. “Hakane fa Amina nima na fara wannan tunanin ga abu mai sauƙi sawa zamuyi asa ya tsani Khausar ɗin ya soki shidama in anyi auren bazaku wuce wata uku ba anan zaku tafi india”. Murmushi Amina tayi kana tace. “Eh kuma wannan abu mai sauƙi ne duk da masifar son da yake yiwa Khausar tun tana ƙarama amma yau ɗin nan tun da muka zauna tsawon zaman mu ya sake min fuska kamar zai iya maraba da duk abinda naje masa dashi”. Cikin jin dadi ta saki wani murmushi tare da cewa. “Tun da muka zauna yau ko yawan kiran sunan Khausar da yake yau be yawaita ba Ummah”. Ajiyar zuciya Hajiya Bunayya ta sauƙe kana tace. “Bari zamu duba mu gani sannan zamuyi magana akai ai ɗazun muka rabu da Jameel da wannan ɗan banzan Moddibon ko yaushe ka gansa da Jallabiya kamar ɗan Larabawa”. Dariya Amina ta fashe dashi kana tace. “Aini shiyasa Samira Sani ke bani mamaki da take son Moddibo me yake dashi meya mallaka komai fa idan kika ganshi dashi sai dai idan Malam Jameel ne ya bashi kullum yana nan acikin Jallabiya bashi da kayan daya wuce Jallabiya ko motar da yake hawa daga kin gani kinsan mahaifin Malam Jameel ne ya saya mishi”. Ta gumi Hajiya Bunayya tayi kana tace. “Ikon Allah shi kuma haka yake ashe se Uban faɗin rai kamar ɗan ƙaruna saboda arziƙi yana abu kamar mai rawani gashi da uban kwarjini”. Tsaki Amina taja kana tace. “Ko sutura kika gansa dashi sai dai in Malam Jameel ne yasaya mishi saboda duk yawanci kayansu iri ɗaya ne na rasa Meyesa Samira Sani take son shi koda yake inaga tsabar kyansa da ƙwarjinsa take so”, Sai kuma ta gyara zamanta tare da taɓe baki kana tace. “Inba hakaba me abin so ajikin talaka faƙiri komai sai aboki ya masa, arayuwa gashi ba kuɗiba se shegen jijji da kai da taƙamar banza da ɗan karen ƙasaita”. Dariya Hajiya Bunayya tayi tare da kallon Amina kana tace. “Nima kaina abin ya ban dariya Amina da Hajiya Lami tazo tana ta haukan bin bokaye akansa yaron da ko wa'azin sa kake kallo yana cikin Jallabiya da Hirami kamar rainon Saudi”. Dariya Amina tayi kana ta taɓe baki tare da faɗin. “Ai dai kam ni dai mai ruwana su suka sani mu dai yanzu mun canza shekarar mu daga kan Malam Jameel zuwa Uncle Naseer”, murmushi ta saki tare da kallon Hajiya Bunayya kana tace. “Idan kuma za'a tayi akansu su biyun muna raba ƙafa da duk wanda yazo tun da duka Iyayen su nada arziki kuma suma suna dashi duk kansu babu wanda yayi karatu aƙasar nan ko wannensu mijin nunawa sa'a ne da zaran na auri ɗaya daga cikinsu zan zama big Girl acikin garin nan”. Acan ɓangaren Gimbiya Dadu kuwa Uncle Naseer ne zaune akan 2sitter hannunsa riƙe da wayarsa yana latsawa Gimbiya Dadu na zaune kan Sallaya tunda ta idar da maghariba bata motsa ba suna taɓa hira jefi-jefi. Cike da nutsuwa Lamiɗo yayi sallama ya shiga, tare da miƙawa Uncle Naseer hannu sukayi Musabaha kana ya gaishe da Gimbiya Dadu. Cikin sanyin Murya Lamido ya kalli Gimbiya Dadu kana yace. “Ɗazu fa Ramadan ya gamu da hatsari ya karye”. Da sauri Uncle Naseer ya ɗago kansa kana yace. “Subhanallah³ ikon Allah”. Gimbiya Dadu ma cikin sauri ta ɗago kanta tare da kallon Lamiɗo cikin yana yin damuwa tace. “Subhanallahi bari idan na idar da Sallar Isha'i zanje in duba sa”. Miƙewa Uncle Naseer yayi tare da cewa. “Bari naje na dubasa”. Ya faɗa tare da ficewa. Kai tsaye sashen Mommy ya nufa bakinsa ɗauke da Sallama Ahankali Idanunsa suka sauka akan Khausar dake zaune gaban Ramadan kallon falon yayi yaga ba kowa sai su kadai. Ahankali Khausar data ji Sallamar sa ta juya ta kallesa. Cike da duniyan ci ya sakar mata da mayaudariyar murmushi kana ya kashe mata ido ya wani langwaɓar da kai tare da Shagwaɓe fuska kana yace. “Ya dai Matas?”. Shiru Khausar tayi tare da yin ƙasa da kanta cike da mamakinsa aranta tace Uhmmm Uncle Naseer da tsaurin Ido duk abinda ya aikata ashe zai iya zuwa inda nake. Cikin rashin damuwa ya matsa kusa da ita idanunsa akan Ramadan yace. “Ayyah Ramadan sorry Allah ya sawwaƙa³”. Kai Ramadan ya gyaɗa kana yace. “Ameen Uncle Naseer”. Hannun Ramadan ya riƙe tare da cewa. “Me kakeso in kawo maka”. Kallonsa Ramadan yayi tare da cewa. “Komai ma ka siya min ina so Uncle Naseer ”. Kai ya gyaɗa tare da cewa. “Toh Autan Mommy”. Ahankali Naseer ya juya ya kalli Khausar da Idanunta ke kan Ramadan ya narkar da murya tare da faɗin. “Mommy fa?”. Kamar ba zata ce komai ba sai kuma tace. “Ta shiga ciki tana Sallah Isha'i ne”. Jinjina kai yayi kana yace. “Ayyah Allah ya bashi lafiya”. Ta lumshe Idanunta tare da cewa. “Ameen ya Allah”. Ahankali ya juya gareta tare da gyara zamansa akan rock ɗin kamar yatsun hannunsa zasu taɓa yatsun Ƙafarta. Ya karyar da kai tare da sanyaya muryarsa kana yace. “My dear yau kusan kwana uku kenan koda naki ra wayar ki bata shiga idan wani laifi na miki sai ki faɗa min laifina in baki haƙuri duk da cewa ina da yaƙinin bani nayi miki laifa kece kikayi min laifin, gashi ke kuma baki iya bada haƙuri bako”. Saurin Kallonsa Khausar tayi tare da maimaita bani nayi miki laifi ba aranta. Kamar yasan tunanin da take ya jinjina kai tare da narkar da murya kana yace. “Yes My Khausi Kece kika yi min laifi amma baza kiban haƙuriba to naji na amshi laifina. Ni zan baki haƙuri duk da cewa kin ɓata mana aiki”. Sai kuma ahankali ya juya ya kalli ƙofar Bedroom ɗin Mommy kana ya kalleta duk ya koma kalar tausayi kana yace. “Kin ɓata mana aiki My Khausi baki damu da rayuwata ba ke baki damu da in mutu ko ina rayu ba abinda na faɗa miki ai ba jini kawai ake buƙata ba tunda ba Jinin mutum kawai ba jinin ma na Period ɗin mace magani za'a haɗa min”. Ta gefen ido ya saci kallonta tare da fesar da numfashi kana yace. “Amma kika je kikayi min abinda bashi bane, Wallahi kin yimin muguwar fahimta wallahi ba wani abu bane saboda yanda kika ɓata kikasa na dabba shiyasa aka samu akasin da aka samu”. Anutse Khausar ta ɗago manyan Idanunta dake cike da mamaki ta tsaida su akan sa. Ganin kallon data ke jifansa dashi yasa ya dake tare da langwaɓar da kai kana ya marairaice murya tare da cewa. “Wallahi na rantse miki da Allah My Khausi gaskiya nake faɗa miki ki yarda dani”. Still Ido Khausar ta zuba masa aranta tace Ohhh lalle Uncle Naseer baya tsoron Allah ya aikata abu sannan yazo yana rantsewa da girman Allah saboda baisan girman Allah ba. Hannun Ramadan ya riƙe acikin nasa tare da sake Matsawa gabanta kana yace. “Na rantse miki da Allah My Khausi ban aikata abinda kike zargina ba wallahi tallahi ai babu wani abu sama da Allah?”. Wani irin kallo ta watsa masa tare da Kallonsa kana tace. “Ni dai awajena da duk wani Muminin duniya babu wani abu sama da Allah. Amma awajen matsafi yana da abu da yake ganin zai bashi abu sama da Allah yana da dodon tsafi! Kuma dama yawan rantsuwa a mgn ai masiface”. Zare Ido Uncle Naseer yayi cikin yanayin ruɗewa ya kalleta tare da cewa. “Innalillahi wa'inna Ilahi rajiu'n Khausar!, Khausar!!, Khausar!!! Nine matsafi?, Hasbunallahu wani'imal wakil, ya Salam Khausar Ashe dama kallon da kike min kenan?. Kai cona da wannan zargi da matar aurena take min”. Lokaci ɗaya jikin Khausar yayi masifsr sanyi kallon fuskarsa tayi taga duk yanda ya wani susuce aranta tace To Uncle Naseer ko dai dan naji tsoron abin ne amma kayi haƙuri na zarge ka akan abinda baka aikata ba. Uncle Naseer kuwa jin bata ce komai ba yasa ya sake narkar da murya tare da cewa. “Sam ban taɓa zaton zaki yimin irin wannan mummunar fahimtar ba, My dear koda ace ina tsafi tasirin soyayyarki ba zaisa inyi tsafi dake ba shin idan nayi tsafi dake dawa zan rayu? kece rayuwata My life is nothing without you Khausi”. Dai-dai lokacin Mommy ta fito daga Bedroom.Jin motsin fitowarta yasa Uncle Naseer ya juya tare da dai-dai-ta nutsuwarsa kana yace. “Mommy ya mai jiki ashe abinda yafaru Allah ya sawwaƙa”. Ba yabo ba fallasa Mommy tace. “Ameen mun gode”. Kana ta nufi kichen tare da cewa. “Khausar zo muje mu ƙara sa aiki”. Ahankali Khausar ta kalleta tare da cewa. “Toh”. Mommy kana ta miƙe idanu ya zuba mata har ta ɓacewa Kallonsa. Ajiyar zuciya ya sauƙe tare da miƙewa ya fita. Acan ɓangaren Moddibo kuwa Anutse suka fito daga masallaci bayan sun idar da Sallar Isha'i suka nufi gida suna shiga coumpund ɗin M Jameel ya tsaya. Anutse Moddibo ya juya ya kallesa tare da cewa. “Ya dai J”. Lumshe idanu M Jameel Yayi kana cikin sanyin Murya yace. “A.J muje wajen Ummi mana nayi missing ɗin ta”. Kallonsa Moddibo yayi kana yace. “Kai J ina yau da safe ma kafin muje makaranta sai da muka biya?”. Kai M Jameel ya gyaɗa kana yace. “A.J Ina son ganinta ne wallahi A.J inajin zanyin Aure kwanan nan”. Cike da Mamaki Moddibo ya juya ya kallesa kana yace. “Aure J?”. Kai M Jameel ya gyaɗa kana yace. “Eh zanyi Aure”. Jinjina kai Moddibo yayi kana yace. “Toh babban magana J wannan magana ce mai girma ai mushiga daga ciki muyi ta”. Girgiza kai M Jameel Yayi kana yace. “A'a mushiga mota dai muje muyi ta agidan Ummi”. Wara Ido Moddibo yayi tare da saurin kallon M Jameel kana yace. “J baka da kunya agaban Ummi?”. Murmushi M Jameel Yayi tare da faɗin. “A.J ni kake cewa bani da kunya ba gwara niba cewa nayi inason Aure, kaifa jikinka ne ya nuna kana son Aure na riga dana fadawa Innayi na faɗa mata komai na kuma zaɓa maka matar da zaka aura ma”. Cike da mamaki Moddibo ya juya ya kallesa tare da sakar masa da murmushi kana ya shafa sajensa tare da cewa. “Iyeee sannu Babana”. Dariya M Jameel Yayi kana yace. “Ayaaa kana wasa ne?, Wallahi da gaske nayi maka zaɓin mata kuma na faɗawa Innayi sannan ta aminta da hakan kana na shaida mata cewa A.J ɗina yana ɓuƙatar Aure”. Juyawa Moddibo yayi ya kallesa tare da Matsawa kusa dashi kana ya ɗan mari fuskarsa. M Jameel kuwa dariya ya fashe dashi wanda ya bayyanar da Fararen haƙoransa kana ya shiga tsinkar fulawar dake wajen yana sunsunawa tare da watsa su sama ga hasken farin wata da da gloves ɗin ya haska wajen. Moddibo kuwa idanu ya zubawa M Jameel yana sakin murmushi akai-akai wani irin amintaccen kyau M Jameel ya masa fuskarsa kuwa sheƙi da ƙyalli takeyi more especially gishinsa, lumshe idanu Modibbo yayi kana Aransa yace. “Masha Allah J kayi kyau sosai baka taɓa yin kyau irin na yau ba”. M Jameel kuwa still dariyar ya cigaba dayi yana mai buɗe hannayensa tare da cewa. “Allah ko A.J nayi kyau, kace inje amaryata ta ganni”. Ahankali Moddibo ya sauke Ajiyar zuciya tare da cewa. “Au ashe mgnar ta fito fili.” Cikin sakin yalwataccen murmushin da yasa kyawawan haƙoransa bayyana ya gyaɗa mishi kai. Shi kuwa Modibbo a hankali yace. “Sosai ma kuwa J kayi kyau, fara'a nayi maka kyau idan kana dariya kana kyau sosai”. Ahankali M Jameel ya ɗago ya kallesa still Yana cigaba da dariyar yace. “Ai kaima in zaka yi fara'a haka yana maka kyau A.J”. Girgiza kai Moddibo yayi har zuwa lokacin da murmushi afuskarsa yace. “Bazan iya dariya yanda kake yi haka ba J”. Wara Ido M Jameel Yayi kana cikin dariyar yace. “Zaka iya A.J”. Harɗe hannunsa yayi a ƙirjinsa tare da ɗan jingina da jikin mota, kana ya zubawa M Jameel ɗin idanu yana kallon yadda yaketa dariya har maƙolloton wuyanshi yana ɗan haurawa sama kana ya yi ƙasa, sannan haƙoransa nata sheƙi. Innayi ce ta fito daga sashen ta tare da kallon M Jameel kana tace. “A'a Jamilu yau mai ya maka daɗi haka?”. Cikin dariya sosai ya kalli Moddibo kana ya nuna masa saitin Dick ɗin sa da ido. Da sauri Moddibo ya sunkuyar da kansa tare da kallon inda M Jameel ya nuna da sauri ya lumshe Idanunsa ganin yanda Dick ɗinsa ke miƙe tun ranan da abin ya faru tsakanin sa da Khausar har yau Dick ɗin sa bai sake kwanciya ba koda na second ɗaya sam yaƙi kwanciya ya koma Normal yanda yake cikin dabara ya sanya ƙafarsa ɗaya agaba ɗaya abaya ya matse cinyarsa kana ya cije lips ɗin sa. Wani sabon dariya M Jameel ya fashe dashi tare da riƙe cikinsa kana ya kalli Innayi tare da cewa. “Wayyo Allah cikina hahahaha khhykhy Innayi wai dan nace masa na zaɓa masa mata shine yake cewa, nine Babansa kuma na faɗa masa akan na faɗa miki cewa wallahi Aure yakeso ya girma yanzu shine yake wata magana Innayi ki faɗa masa bana zaɓa masa mata ba?”. Murmushi Innayi tayi kana tace. “Sosai ma”. Moddibo kuwa sajensa ya shafa tare da kallon su kana yace. “Iyeee kune ma masu tsara min rayuwata toni nace muku ina bukatar aure ne?”. Still cikin ƙyelƙyala dariya sosai M Jameel yace. “Ai bai sai kafaɗa da bakin ka ba A.J dama ai body language ɗabi'ar kace to ganganar jikinka ta faɗa min kana son Aure”. Moddibo kuwa cikin sauri ya juya tare da nufar mota jin M Jameel na Shirin tona masa asiri batare daya juya ba yace. Toh kazo mu tafi Innayi bari muje gidan Ummi”. Kai Innayi ta gyaɗa da murmushi afuskarta tace. “Toh Allah ya tsare”. Bayansa M Jameel yabi tare da buɗe motar yashiga har suka isa gidan da zaran M Jameel ya Kalli Moddibo zaiyi dariya shi kuwa Moddibo sai ya sakar masa da murmushi. Suna isa Moddibo yayi Parking suka fita akan baranda suka hango Ummi hannunta riƙe da kayan shanya da alama akan igiya ta ɗebosu, ƙara sawa Moddibo yayi kana yace. “Ummi kawo in karɓa miki”. Miƙa masa yayi. Cike da so M Jameel yace. “Umminaaa”. Kallonsa Ummi tayi tare da ƙara sa shiga falon ya suka biyo bayan ta atare. Akan capet Ummi ta zauna tare da jingina bayanta da jikin kushin kana ta miƙe ƙafafunta ahankali Moddibo ya zauna daga gefenta tare da ajiye kayan wankin ganin kayanta ne yasa ya fara ninkewa. M Jameel kuwa ahankali ya kwanta tare da ɗaura kansa akan cinyar Ummi kana ya ɗaura ƙafa ɗaya kan ɗaya kana ya lumshe Idanunsa tare da cewa. “Ummina kenan”. Ahankali Ummi ta juya ta kalli Moddibo kana ta mayar da kallonta kan M Jameel sai kuma ta ɗaga kanta ta kalli haɗeɗɗen agogon dake manne abango kana ta sauƙe Idanunta ƙasa tare da cewa. “Ayana yin garin nan da yake ga alamun yau akwai hadari sannan baku zo da wuri ba dubi time fa har kusan 8:30 kodai zamu kwana ne?”. Murmushi M Jameel Yayi tare da ɗago kai ya kalleta kana ya langwaɓar da kai tare da cewa. “Ummi dana fi kowa farin ciki ace yau gani gaki muna kwana gida ɗaya”. Juyawa yayi ya kalli Moddibo kana yace. “Shiyasa ma nake faɗawa A.J nifa Aure zanyi”. Cikin sauri Ummi ta juya ta kallesa kana cike da Mamaki wannan shine karo na biyu da yake faɗa mata Kalmar yana son Aure Girgiza kai tayi kana tace, “Jamiluuuu”,Ta faɗa kai tsaye ta rasa Meyesa acikin kwanakin take kiran sunan sa kai tsaye. Dariya M Jameel ya fashe dashi sosai yake ƙyalƙyala dariya harda kaɗa ƙafa. Asma'u da Bashir kuwa jiyo sautin dariyar sa yasa suka fito daga Bedroom tare da zama daga gefensu cike da girmamawa suka gaishesu atare. Ahankali ya kalle tare da sakar musu da murmushi kana yace. “Ƴan ƙanne na”. Sai kuma ya juya ya kalli Ummi dake murmushi kana yace. “Wallahi Ummi dagaske aure nake so”. Wara Ido Asma'u tayi cike da farin ciki ta kalli M Jameel kana tace. “Kai Alhamdulillah gaskiya munji daɗi”. Murmushi M Jameel yayi kana yace. “Aikam dai Asma'u munji daɗin mu zan ginawa Ummina da Malam side ɗin su na musamman in saka su acikin”. Sai kuma ya numfasa tare da lumshe idanunsa kana yace. “Sannan ingina miki ɗakin ki in zuba miki kayan masu kyau sannan Bashir ma ingina mishi side dinsa da ban da daddare kafin inyi bacci inzo inyi hira da Ummina inganta ta ganni kana kullum idan gari ya waye daga na dawo daga masallaci in biya inga Ummina ta ganni kana ta bani shayinta mai daɗi Insha”. Cike da jin daɗi Asma'u ta kallesa kana tace. “Allah yasa Yah Jameel”. Lumshe Idanunsa yayi kana yace. “Hmmmm!”. Kansa Ummi tashafa cike da ƙaunarsa tace. “Ameen”. Moddibo kuwa ahankali ya zuba musu Idanu yana kallon su cike da burgewa. Ummi kuwa ahankali take shafa kan M Jameel kana tace. “Kai ko kunya baka ji ƙato da kai kazo ka kwanta min akan cinya na!?”. Ta ƙarashe maganar tana shafa yalwataccen sumar kansa. Murmushi yayi kana yace. “Uhmmm Ummina idan ban ɗaura kaina akan kiba to akan wa zan ɗaura? Abinda ma ya kusa ƙare wa hmm”. cikin sauri tace. “Ya kusa ƙare wa kamar ya!?”. Murmushi yayi kana yace. “Idan nayi Aure mana ai shikenan na samu sabon cinya”. Girgiza kai Moddibo yayi tare da kallon M Jameel kana yace. “Mtssss J Allah ya shiryeka”. Miƙewa M Jameel Yayi tare da kallon Ummi kana yace. “Ummi nida A.J rana ɗaya za muyi Aure, nida Innayi mun zaɓa mishi mata, amma sai idan nazo ni kaɗai zan faɗa miki sai mugama magana tsakanina dake”. Wara ido Ummi tayi tare da kallon Moddibo kana tace. “Allah ko”. Kai ya gyaɗa mata yana dariya ganin hararar da Moddibo ke wurga masa kana yace. “Eh”. Sha ɗaya saura suka yiwa Ummi Sallama kana suka tafi suna isa gida suka shiga falon M Jameel har ya juya da niyyar shiga ɗakinsa da yake kwana ya fasa yabi bayan Moddibo. Ahankali Moddibo ya juya ya kallesa tare da cewa. “Ya dai J?”. Murmushi M Jameel Yayi kana yace. “Yau tare zamu kwana”. Kai Moddibo ya gyaɗa kana ya wuce ciki. Tunda Moddibo ya fito daga toilet ya zauna agefen gado tare da dafe kansa da hannu biyu har yanzu bai janye yayinda Jameel kuwa ke ciki. Ahankali M Jameel ya fito daga toilet ɗin. Yana mai tsane suman kanshi da mini towel Idanunsa suka sauƙa akan Moddibo daya dafe kansa da hannu biyu. Cike da kulawa yace. “A.J ya dai?”. Ahankali Moddibo ya ɗago kansa. M Jameel kuwa kallon yanda Idanunsa suka kaɗa suka jawur yayi kana lips ɗin sa na rawa yayin da jikinsa ke ɓari kamar mai jin sanyi. Cikin sauri M Jameel ya matsa kusa dashi kana yace. “A.J ya dai?”. Cikin yanayin damuwa da raunin murya Moddibo ya kallesa kana ya miƙe tare da yin wani irin fitinenne miƙa Atake A ɗin sa ya Miƙe tsaye baki ɗaya jikinsa rawa yake idanunsa sun kaɗa sunyi jawur tuni lips ɗin sa ke rawa tamkar mai jin zazzaɓi. Wani irin tausayinsa ne ya kama M Jameel Cike da tausayawa yace. “A.J ya dai?”. Cikin yanayin tashin hankali Moddibo ya Girgiza masa kai kana cikin raunin murya yace. “J ga halin danake c....! *Littafin SAKAYYAH dai na kuɗine 1k ne kacal ki biya ki karanta cikin aminci 0661110170 GTBank AISHA ALIYU GARKUWA.* *By* *GARKUWAN MARUBUTA* [30/07, 1:40 PM] Halimatu A/rahman Sadeeya: *Al'bishirunku Ma'aurata, GA GARKUWAR KU nan tafe muku da tsarabobi na musamman gareku ma'aurata daga cibiyar mgnin mata mai taken GARKUWAR MA'AURATA* NI DAI AYSHA ALIYU GARKUWA. Ina matukar mamakin wani irin lokaci da ya riske mu mai wahalallan fassara. Kullum dai magana daya ce, akan ma’aurata, fada, rashin jituwa, mutuwar aure, akan kuskure kalilan, rashin kula, rashin yi wa juna uziri. Toh wai duk me ya janyo hakan? Na zurfafa a tsananin tunani hakan ya tilasta min bincike mai tarin yawa wanda ya kai ni ga gano inda matsalar take? Shin yar’uwa ke macece amma kin san wacece mace ku? Kin san me ake kira mace kuwa? Mace ita ce matar da take zama iyali a wajan namiji ta zame masa bango, sanyin idaniyarsa, ta zame masa gata da farin cikin rayuwarsa ta zame masa ruwa abar kore ƙishinsa ta zame masa mayafi mai karesa daga gigitar kadaice, ta kuma dorar da mijinta kan turbar gaskiya, ta kashe masa jiki da salonta ta rikita shi da baiwa da ni’imar da Allah ya bata idan har ta san hanyar mayar da kanta sabuwa dal awajanta, wato kullun takasance masa tamkar amarya har ya kasa tantance daren amarcinsu da sauran dararen rakun rayuwar su. Wannan ita ce mace. Ina da wata saukakkar hanyar da zaki zama abar so da kulawa da soyayya a wajan mijinki ta hanya mafi sauki, 09097853276 hanyar ita ce ki gwada amfani da kayana na gyara ki gani, ina mai tabbatar miki da in sha Allahu sai kin dara da murna sai kuma kin gode min. Kayana kaya ne da aka yi shi da zallan itacanmu na gado marasa illa a cikin jikin dan adam musamman mace, kaya ne da suke taimakawa (sex hormones 😍) dinki. Misali kina kallon India😘, hollywood, Asian film🥰 kina ganin yanda mazansu ke nunawa matansu tsananin soyayya kamar su ba su kyautar ransu!? Saboda me hakan? Saboda suna sadaukar da lokacinsu wajan gyara jikinsu da kayan da ke tsattsafo da ni’ima cike da tsukewa, kayan nan kuma ana yinsu ne zallar magungunan gargajiya wanda ba su da illa domin haɗine na ingantattun itatuwa da yayansu. Ina baiwar Allahn da miji ke daure mata fuska babu hirar arziki? Zo ki ji yar’uwa zan baki gumbata da zallar gari wanda aka yi su da nagartattun itacen da ke da matukar amfani a jikin mace. Gubar ciko, gumbar tsalle dole, gubar da ba'a baiwa mai kishiya, garin maɗi, garin mallaka, tsumin goron tula, tsumin tsartai, tsumin maratsi, pala-pala butar sirri, kwanon k’asaitacciyar mace, furar mata madararta gareki Hajia takenta sha yanzu mgni yanzu, Ina mata masu fama da sanyi? Sanyin mara ki zo na hadaki da magani na na sanyi wanda yake wanke mara ya fitar da duk wata cuta da ke samun mazauni a wajan. Ina da ciccibi mai kyau. Ina da hadin amare mai kyau wanda zai gyara yarinya ya kankaro mata kimarta akwai hadin mai jego wanda muke yinsa na asali inada kekkyawan Hadi maida tsohuwa yarinya. Akwai daya bangaren wato *KAMSHI* Kimarki gyaranki da kamshinki. Matan da suka gane suka san yanda za su kankaro da mutunci su ne masu amfani da kayan gyara da kuma sanyaya jikinsu da kamshi, ina da turaren wanka da na bandaki na daki na jiki da na kaya dana tsuguno kamshin turarena na dabam ne mai sanyaya zuciyar wanda ya shaka ina da kayan kamshi na amarya da na maijego da na uwargida da dukkan macen da take kokarin mayar da kanta mai daraja a idon kowa ta zamo sarauni a idon mijinta, akwai shu'umar humra, sayan na gari maida kuɗi gida, banda karanta yayin gyara Hajia. Zaku iya samun kayyakina a duk garin da kike, zakiyi min mgn ta whatsApp number na 09097853276 domin yin zaɓinki, ko karin bayani, zaki tura kuɗin ta account na 0005388578 Jaiz bank AISHA GARKUWA ALIYU in mun gama mgna zan sa miki kaya a mota yazo duk garin da kike, in baki shirya saya yanzuba Please kada mu wahal da juna ki bari sai kin shirya kafin kiyi min mgn. 🤝🏻🥰😘 Daga taku AYSHA ALIYU GARKUWA *(GARKUWAR MA'AURATA)* Isrehjɗɗ. Acan Falon Moddibo kuwa zaune yake akan 2sitter hannunsa riƙe da Kofin Tea yana sha time to time zai ɗaga kansa tare da kallon agogon dake manne abango ahankali ya gyara zamansa tare da kurɓan tea dake tiriri ya lumshe idanunsa tare da buɗe su akan agogon cinyarsa ya matse da ƙarfi har saida yaji jikinsa na rawa, ƙara matse jikinsa yayi sabida yadda yake jin M ɗinsa na miƙewa yana harbawa cike da zalama, ɗan gajeren tsakiya yaja, cikin sanyin murya a fili yace. “J har yanzu baka dawo ba”. Yayi mgnar kamar Jameel ɗin na gabansa. Sai kuma ahankali yasa hannunsa tare da laluɓar wayarsa a aljihun sa na hagu da dama jin babu yasa yaja siririn tsaki tare da miƙewa cikin wani irin masifeffen kasala da sanyin jiki mai kashe ilahirin gaɓɓai ya nufi bedroom ɗinsa a kuma lokaci ɗaya zuciyarsa ta buga tare da tsinkewa da masifaffen ƙarfi, da ƙyar ya iya ɗaga ƙafarsa na dama kana ya taka ya shiga Bedroom tare da furta. “Hasbunallahu wani'imal wakin”. Jin yanda zuciyarsa ke cigaba da bugawa cikin yanayin tsinkewar zuciya da sanyin jiki ya ɗauki ƙaramar wayar tasa, kana ya dawo falon ya zauna tare da shiga Call log zai kira M Jameel sai kuma kiran Malam Arɗo yashigo wayar sa. Zubawa screen ɗin wayar ido yayi tare da jan siririn tsaki kamar ba zai ɗaga ba sai wata zuciyar tace ka ɗaga mana kasan menene Uzirinsa ajiyar zuciya ya sauƙe tare da picking. Acan ɓangaren Ummi kuwa zaune take a falonta kan kujera 3sitter tayi ta tagumi da duka hannunta biyu, kana ta tsirawa waje ɗaya Idanu yayin da ƙirjinta ke bugawa da masifar ƙarfi zuciyarta na tsinkewa yana bada sautin dif-dif-dif lokaci ɗaya taji wata muguwar kasala na rufe mata jiki haka nan take jin zuciyarta na tsinkewa. Jiki a mace Asma'u ta fito daga kichen hannunta riƙe da Plate ƙara sawa falon tayi Idanunta akan Ummi data zabga tagumi ta zauna akan 1sitter tare da cewa. “Ummi har yanzu baki kwanta ba?”. Ajiyar zuciya Ummi ta sauƙe tare da fesar da numfashi kana ta gyaɗa mata kai tare da cewa. “Eh Asma'u ban kwanta ba”. Cike da kulawa Asma'u ta ɗaga kanta tare da kalli agogo, tare da cewa. “Ummi kalli fa har sha ɗaya ta wuce me kikeyi afalo ke kaɗai shiru ga Abban mu yashiga tun ɗazu”. Lumshe Idanu Ummi tayi still zuciyarta na tsinkewa kana tace. “Babu”. Numfashi Asma'u ta fesar tare da ajiye cokalin dake hannunta tace. “Toh Ummi ko dai baki da lafiya ne?”. Kallonta Ummi tayi tare da girgiza kai. “Lafiyata ƙalau Asma'u”. “Ayyah Ummi am to mai yasa baki kwanta ba kin zauna shiru ke kaɗai dubi yanda kika yi tagumi da hannu duka bibbiyu”. Cewar Asma'u. “Ban sani ba Asma'u ba wai bani da lafiya ba amma ina jin jikina wani iri bai min daɗi ba ina jin zuciyata na tsinkewa sannan ga wata kasala data rufe ni”. Ido Asma'u ta zuba mata kamar mai son gane wani abu sai kuma tace. “Toh Ummi ki riƙa maimaita Hasbunallahu wani'imal wakin mana kuma may be rashin bacci ne kinga jiya kwana mukayi muna hira ba kisamu kinyi wadataccen bacci ba, sannan yau da safe ma baki samu kinyi wani ishesshen bacci ba”. Gyara riƙon da taiwa plate ɗin tayi kana taci gaba da cewa. “Har yanzu ma baki samu kinyi Ummi, kiyi ƙoƙari kije ki kwanta Insha Allah zakiji dama dama”. Kai Ummi ta jinjina tare da cewa. “Toh ki maida Plate ɗin kichen idan kin gama sannan ki rufe ƙofar kichen ɗin kana kizo ki rufe mana ƙofan falon”. Kai Asma'u ta gyaɗa tare da cewa. “Toh”. Ta mike tare da ajiye Plate din ta kife Sauran abincin sannan ta rufe ƙofar tare da murza mukulli ta dawo. Still zaune ta samu Ummi tayi tagumi. Cike da kulawa tace. “Ummi kije ki kwanta dan Allah kiyi baccin”. Ahankali Ummi ta ɗago ta kalleta tare da sauƙe ajiyar zuciya kana tace. “Toh kije Insha Allah yanzu zan kwanta”. Kai Asma'u ta gyaɗa kana ta wuce Bedroom ɗin ta Ummi kuwa kasa tashi tayi ahankali ta lumshe Idanunta tare da komawa ta kwanta akan kujeran still zuciyarta na cigaba da tsinkewa tana mai maimaita kalmar Hasbunallahu wani'imal wakin aƙasan ranta. Acan ɓangaren Moddibo kuwa yana Picking call ɗin yakai kunnensa tare da cewa. “Assalamu Alaikum”. cikin sanyin murya M Arɗo ya gyara zaman wayar akunnensa tare da cewa. “Wai yanzu yaran nan tsakanin ku da Allah kun bar batun karantarwa Amakarantar nan kenan?”. Anutse Moddibo ya lumshe Idanunsa kana ya buɗe su cikin yanayin kasala da tsinkewar zuciyar da yake ji ya gyara zamansa tare da cije lips ɗinsa na ƙasa yace. “Toh ka asamsa Sallamar da nayi maka mana Before ka fara ƙorafi da zakayi”. Girgiza kai Malam Arɗo yayi tare da cewa. “Toh Wa'ailaikum salam kune ai baki ɗaya kuke son caza min kai, baki ɗaya satin nan yashiga har ya fita amma baku zoba toh gashi yau jumma'a gobe Asabar za akoma shiyasa nace bari na kira ku kada ace baku zoba”. Iska mai zafi Moddibo ya fesar daga bakinsa tare da shafa sajensa kana ya lumshe idanunsa tare da cewa. “Gaskiya baza mu zoba”. Asanyaye Malam Arɗo yace. “Toh meyesa”. Muskutawa Moddibo yayi tare da gyara zaman wayar akunnensa kana yace. “Ai mun riga da mun gama yi maka magana kayi haƙuri kawai ”. “Amma kunsan ina son koyar wanku Amakarantar nan ina jin dadin zama daku sannan ɗaliban ma suna jin daɗin koyarwanku, makaranta na ya cigaba adalilin kune kada kuyi min haka”. “Malam kayi haƙuri da akwai Uzurin da yake gaban mu, wanda yafi wannan na tabbata badan wannan Uzurin ba babu dalilin da zaisa mubar koyar wa Amakarantar”. Cikin sanyi murya Malam Arɗo ya sauƙe Ajiyar zuciya kana yace. “Toh shikenan tunda abin ya zama haka dole in sawa zuciyata haƙuri amma kusa marmin wasu Malamai masu Hazaƙa, duk da nasan da wuya asamu kamar ku tabbas nasan nayi rashin zaƙaƙuran Malamai kamar ku”. Kai Moddibo ya gyaɗa kana cikin sanyin murya yace. “Toh ba matsala zamu yi kokarin hakan”. Cikin sanyi Malam Arɗo yace. “Toh Nagode saida safe”. kana ya katse wayar. Moddibo kuwa cikin sauri zuciyarsa ya cigaba da bugawa yana bada sautin dif-dab-dif-daf ahankali ya ɗago wayar da niyyar kiran M Jameel cikin wani Irin yanayi ya dafe saitin ƙahon zuciyarsa jin yanda yake bugawa da azabebben ƙarfi yana cigaba da bada sautin dif-dif-dif rintse idanunsa yayi still hannunsa na dafe da saitin ƙahon zuciyarsa. Acan ɓangaren Gimbiya Bunayya kuwa har Misalin ƙarfe sha biyu da minti biyu na dare Uncle Naseer da Amina na zaune akan 2sitter suna hira. Yayin da ita kuma ke kwance a Bedroom ɗin ta kunneta maƙale da waya tana Magana da Hajiya Lami. Murmushi Hajiya Bunayya tayi tare da cewa. “Hajiya Lami ni dai yanzu Alhamdulillah buƙata ta biya hankalina ya kwanta, yanzu batun soyayyar Amina da Naseer ya kankama yayi zurfi”. Atake fara'ar dake fuskanta ya gushe ta mike ta zauna tare da cewa. “Yanzu kuma hankalina ya koma kan ƴaƴan wannan shegiyar matar mai kama da Mayyar wannan yaro mai ƙwala-ƙwalan ido daya karye nake son kawar dashi tun da shi wancan mai kama da Brolas ɗin Uwarsa ta shayar dashi saɓani, tunda kinga wannan hatsarin ma shi na shiryawa abi takansa amma, ba'a samu babban ba akabi takan ƙaramin”. Sai kuma ta sauƙe numfashi tare da jan dogon tsaki kana tace. “Dole saina koma na samu boka Kar'uzu da maganar ayi duk abinda za ayi nikam Haiydar shine babban matsala ta tunda shi Ramadan shine ƙarami akan Aminu, babu yanda za ayi Aminu na raye aɗauki Sarauta abawa Ramadan dole dai sai ɗana ɗin dai”. Cikin sauri Hajiya Lami ta katseta tare da cewa. “Kul-Kul Hajiya Bunayya kada kiyi la'akari da wannan ƙaramin tunanin naki, ba kiji Malam Bahaushe na cewa ɗan hakin daka raina shike tsole maka Ido ba?. To ki rufa wa kanki asiri ki kawar dasu duka biyun hankalinki ya kwanta ki samu nutsuwa da salama aranki”. Kana ta saki wani murmushi tare da cewa. “Kinga idan kika gama dasu ɗaya ce zaki samu nutsuwa akanta itace Raudat da kuma Khausar. Kinga Khausar kuwa ba ƴar gidan bace babu yanda za ayi agola tavi gadon Sarauta koda na mijine bare kuma mace. Raudat kuwa ƙarama ce kuma mace. Amman Haiydar da Ramadan dai kaudasu, da kike batun Ramadan shine ƙarami a kan sulaiman, sau nawa manyan Yayu ke zaune ake bawa ƙannen su Sarautar, ni dai shawarar da zan baki yanda zaki gama da Haiydar haka zaki gama da Ramadan”. Jinjina kai Hajiya Bunayya tayi tare da gyara zaman wayar akunnenta kana tace. “Haka ne fa kuma aini duk wannan tunanin bai zo min ba, atunanina idan na kawar da Haiydar shikenan”. Girgiza kai Hajiya Lami tayi tare da faɗin. “A'a tsaya kallon ruwa kwaɗo ya miki ƙafa, har kina wani batun shine ƙaramin akan Aminu ai ba'a wannan zancen kima rufawa kanki asiri, kigama dasu gaba ɗaya to asannan hankalin zai kwanta, ki samu nutsuwa anan ne zaki tabbatar sarauta ahannun Aminu take, ke kuma kin zama Gimbiyar Gembulan Matar sarki Uwar sarki amma muddin ƴaƴan wancan koɗaɗɗiyar matar na nan keda Saurauta saidai hange daga naisa”. Jinjina kai Hajiya Bunayya tayi cike da gamsuwa kana tace. “Aikuwa hakane Nifa duk wannan tunanin bai zomin ba shiyasa nake alfahari dake ƙawata. Insha Allah zanje muyi magana da boka Kar'uzu asan yanda za'a ɓullowa lamarin”. Kai Hajiya Lami ta gyaɗa tare da cewa. “Eh nima Insha Allah gobe idan muka je zan faɗa masa ya tsaida rana da Samira zata fara zuwa wajensa suyi satin, tunda dai yace idan ya kusance tama zai mayar mata da budurcinta ai shikenan”. Atare suka sheƙe da dariyamai cike da farin ciki da annushawa kana Hajiya Bunayya tace. “Ai dai haka yafi shiyasa na yarda da aikin Boka Kar'uzu kamar yankan wuƙa dan sha yanzu magani yanzu ne tun yaushe muke bin boka bursunu tsawon shekaru ba biyan buƙata sai asaran kuɗi”. Jinjina kai Hajiya Lami tayi kana tayi mata Sallama suka katse wayar. Aɓangaren Abban M Jameel kuwa tsaye yake ajikin window falonsa ya tsirawa harabar gidan Ido tun bayan fitar Motar M Jameel ya kasa motsa wa daga wajen. Hajiya Karima data fito daga Bedroom ɗin sa ta dubesa cike da kulawa tace. “Ya dai Alhj tun tuni kana tsaye ana ka gaza motsa sama da awa biyu kenan tun bayan fitar motar Jameel kake tsaye lafiya kuwa?”. Cikin wani irin yanayi ya lumshe idonsa. Haka nan yaji ruwan hawaye na tsats-tsafo masa a hankali ya sauƙe ajiyar zuciya tare da furzar da iska kana yace. “Haka nan dai narasa me nake tunawa awajen nan”. Ajiyar zuciya ta sauƙe tare da dafa bayansa kana tace. “Toh kazo ka zauna mana”. Girgiza kai yayi tare da fesar da numfashi kana cikin sanyi murya yace. “Ina ga ko dan garin dana gani da alamun hadari ne ko yaya ne ban sani ba”. Kai ta gyaɗa tare da cewa. “Toh kadawo ka zauna dan Allah tsayuwar tayi yawa”. Kai ya gyaɗa lokaci ɗaya yaji wani irin masifaffen rauni mai haɗe da bugun zuciya ya rufe sa Atake yaji Idanunsa na tsats-tsafo da ruwan hawaye masu ɗumi yayin da zuciyarsa ya cigaba da tsinkewa jikinsa na mutuwa tamkar ana zare masa laka cikin sanyi jiki yaja ƙafafunsa da yaji sunyi masa mugun nauyi ya zauna akan kujera tare da kwanciya akan 3sitter kana ya lumshe Idanunsa. Cike da kulawa tace. “Ya dai lafiya kuwa kashiga ciki mana?”. Girgiza kai yayi still zuciyarsa na cigaba da bugawa yayinda muryarsa ke ɗauke da rauni yace. “Please Karima ki barni in kwanta inaji kamar kaina na ciwo”. Cikin sauri tace. “Alhj kad dai BP kane?”. Girgiza kai yayi still Idanunsa na lumshe yace. “A'a ba BP na bane bari dai mu gani”. Zama tayi daga hannun kujeran kana tace. “Toh kasha maganin ka kuwa?”. Kai ya gyaɗa tare da cewa. “Eh sosai ma yan zun nan kafin Jameelu ya fita ya bani nasha”. Kai ta gyaɗa tare da cewa. “Eh ƙwarai kuwa hakane toh Allah ya sawwaƙa”. Ahankali yace. “Ameen”, Miƙewa tayi tare da shiga Bedroom ɗin sa ta kwanta. Ɓangaren Moddibo kuwa har Misalin sha biyu da kwata yana zaune dafe da ƙirjinsa dake cigaba da bugawa ahankali ya ɗago kansa tare da shafa gefen wayarsa haske ya bayyana tare da nuna masa ƙarfe 12:15 afili ya furta. “Har yanzu J bai zoba”. Yayi mgnar tare da shiga Call log yayi dearling number M Jameel amma ga mamakinsa sai yaji Swich off. Cikin yanayin damuwa ya dafe kansa tare da cewa. “Ikon Allah lafiya kuwa wayar J arufe?”. Kallonsa ya mayar kan babbar wayarsa tare da ɗauka kana ya fito da ɗaya number M Jameel ya kira Shima still Swich off. Miƙewa tsaye yayi ido a lumshe yace. “Ha'a ya wayar J akashe kuma dai J baya kashe wayarsa, to amma mai yafaru yau wayarsa akashe toh me yake faruwa bayan ya faɗa min yau zai dawo!?”,l. Yayi maganar cikin zulumi “Ya ilahi ya mujabat da'awati, to kuma ko kafin J ya fito sai da ya kirni yace zaije wajen Abba ya sallame sa sannan yazo amma kuma har yanzu bai zoba”. Atake wata zuciyar tace kasani ko yazo suna tare da Innayi suna can suna ƙus-ƙus atake ya amince da abinda zuciyarsa ya raya masa cikin mutuwar jiki ya nufi ƙofan falonsa tare da buɗewa. Wani sanyayyan iska ya hurasa ahankali ya ɗaga kansa sama gani yayi hadari ya fara haduwa sai walƙiya dake haskawa can ƙasa alamun yanzu hadarin ya fara, garin ya danyu duhu sakamakon rashin wuta ga kuma hadarin, ahankali yabi sararin samaniyar da kallo ganin yanda hadarin yayiwa garin zobe kana aƙasan ransa yace to kodai wannan hadarin ne ya hana J zuwa sai kuma yace to kodai yana ɗakin Innayi ya faɗa yana taka step ɗin ahankali. Cikin sauri Innayi ta haske masa ido da touch light mai masifar haske cikin han zari ya Janye hannuunsa dake danne da J ɗinsa ya tare Idanunsa dashi saboda hasken touchlight daya haska masa ido. Cike da kulawa Innayi tace. “Moddibo ya dai lafiya ina zuwa Atsakiyar adaren nan?”. Ahankali ya sake sakƙowa daga kan step ɗin tare da jingina bayansa da jikin filan barandarsa, kana hannunsa na dama na kan flowes dake gefe yace. “Kece fa kike ganinsa tsakiyar dare ne, dudu shabiyu da rabi ne fa yanzu”. Kallonsa tayi tare da cewa. “Tsakiyar dare ne mana Moddibo yanzu fa ƙarfe shabiyu harda rabi ai tsakiyar dare ne, to amma me kafito yi lafiya dai ko?”. Cikin sanyin murya yace. “J ne har yanzu bai zo ba kuma ya fito akan zai zo ma ya kirani awaya kan cewa yanzu zai shiga wajen Abbansa ya masa saida safe ya fito, kuma har yanzu bai iso ba sannan nata kiran layukan sa basa shiga”. Ya ida maganar akasalance. Ajiyar zuciya Innayi ta sauƙe tare da cewa. “Toh dan bai zoba Moddibo ai ba abin tashin hankali bane, kaga yanayin wannan hadarin daya haɗu zai iya hanasa zuwa wataƙil daya shiga wajen Abban nasa zaice dare yayi kuma ga hadari ya bari sai gobe”. Da sauri ya katseta da cewa. “To ai Innayi wayarsa bata shiga fa”. Saurin Kallonsa Innayi tayi tare da cewa. “Ka kira layinsa duka?”. Kai ya jinjina mata. “Eh na kira layukansa duka fa basa shiga”. Cikin yanayin bacci ta kalli Moddibo tare da sakin hamma kana ta aro Jarumtaka tare da cewa. “To ko dai network ne?”. Lumshe Idanunsa yayi tare da Girgiza mata kai kana yace. “A'a ba network bane cemin akeyi akashe kuma fa Innayi J baya kashe wayarsa, ko zai kwanta komai yaya kuma nasan wayar J baya rasa caji”. A hankali Innayi ta rufe idonta jin kamar tsinkewar zuciya ya ziyarci ta. Amma sai ta daure kana tace. “To amma kaga jiya ma kace min wajen Umminsa ya kwana to ko dai yauma yaje canne ne ya kashe wayarsa dan kada kayi ta kiransa?”. Jinjina kai yayi tare da faɗin. “Ok ba mamaki fa bari na kira Ummi”. Cikin sauri Innayi ta kallesa tare da cewa. “Aƙarfe ɗaya saura zaka kirasu?” Kai ya gyaɗa kana yace. “Eh Innayi in dai har wurin Ummi yake nasan yanzu zasu ganshi kamar takwas na dare ne, saboda nasan yanzu suna hira ba suyi bacci ba. Kai Innayi ta gyaɗa tare da gyara tsayuwar ta kana tace. “Toh shikenan ka kira”. Dearling number Ummi yayu. Acan ɓangaren Ummi kuwa kwance take yayin da idanunta ke lumshe cikin tsananin tsinkewar zuciya da kasala jin rurin wayarta yasa ta miƙe firgice cikin yanayi sanyi sanya hannunta na dama ta janyo wayar tare da ƙurawa screen ɗin Ido sunan Moddibo ke yawo. Cikin sauri tare da rawan jiki tayi Picking call ɗin tare da kaiwa Kunnenta batare data amsa Sallamar daya mata ba tace. “Babana Lafiya?”. Cikin ƙoƙarin danne damuwarsa yace. “Ummi lafiya ya naji kamar kin razana?”. Ahankali ta koma ta jingina bayanta da jikin kushin ɗin tare da lumshe idanunta kana cikin wata raunan'niyar murya mai cike da kasala da tsoro ta fesar da numfashi tare da cewa. “Gaba ɗaya ma ai. Arazanen nake Babana”. Moddibo kuwa cikin kasala da mutuwar jiki ya yaja numfashi tare da fesar wa kana yace. “To Ummi me yafaru?”. Buɗe Idanunta dake lumshe tayi tare da dafe ƙirjinta da still yake bugawa kana tace. “Ban saniba amma gaba ɗaya ina jina wani irin gani nan dai kamar mara lfy, kuma ba zance ga abinda yake damuna kai tsaye ba”. Ajiyar zuciya Moddibo ya sauƙe kana yace. “Toh amma Ummi lafiyar ki lau?”. Kai ta gyaɗa masa kamar yana gabanta kana tace. “Lafiya ta ƙalau,Amma Babana lafiya ka kira yanzu?”. Numfashi ya sauke tare da lumshe idanunsa kana ya sake jingina bayansa da jikin step ɗin tare da cewa. “Eh lafiya lau babu komai dama zan tambayeki ne ko dai J yazo yana wurinki ne munyi dashi tun ɗazu akan zai zo har yace min gashi ya fito amma zai sallami Abbansa ne kawai ya taho”. Sai kuma ya lumshe idanunsa tare da cijan lip ɗin sa na ƙasa kana yace. “Amma har yanzu be taho ba, inata jiran sa ko ƙofar gida bamu rufe ba, shiyasa nace bari na kira koya biya wajenki, da yake jiya ma nan ya kwana!?”. Rumtse ida nunta tayi da masifar ƙarfi k cikin wani azabebben tsinkewar zuciya da faɗuwar gaba ta buga hannunta na dama aƙirji tare da cewa. _“Innalillahi wa'inna ilahi rajiu'n. Allahumma Ajirni fii musibati wa'ahlifli khairan min_ bai zo ba kuma yace maka zai zo? Abbansa kaɗai zai Sallama?”. Gyaɗa kai Moddibo yayi tamkar yana gabanta kana cikin raunan'niyar murya mai cike da sanyi yace. “Eh Ummi”. Cikin wani irin yanayi na taraddadin zuciya da rauni Ummi tace. “Ya Ubangiji Allah ka dubeni da Idon Rahma. Ya Allah ka tsare wannan bawan naka, aduk inda yake Alfarman Annabi da Alkur'ani”. Jin salatin da kuma yanayin da Ummi tayi Magana cikin firgici ya farkar da Asma'u, Bashir da Malam Ahmad Aruɗe Asma'u ta miƙe tare da dafe kanta da taji yayi masifar sarawa ta sauƙa daga kan gadon. Acan ɗakin Bashir kuwa Hasbunallahu wani'imal wakin ya furta tare da sauƙa ƙasa kusan atare suka fito falon ko wannensu zuciyarsa na bugawa da kaso tamanin cikin ɗari. Moddibo kuwa cikin sanyu da ruɗu yace. “Ameen ya Allah Ummi ameen ya rabbil Izzati”. Cikin zulumi Ummi ta runtse Idanunta kana tace. “Amma Babana ka kira Abbansa mana”. Numfashi Moddibo ya fesar tare da kallon Innayi data tsaresa da ido cikin yanayin razani yace. “Eh Ummi nayi tunanin kiran Abbansa amma sai nace bari na fara kiranki tunda jiya yazo na, sannan Ummi nasan J baya kashe wayarsa rashin shigar wayarsa nema yafi damuna!”. Girgiza kai Ummi tayi yayinda ruwan hawaye masu masifar ɗumi suka cika kwarmin Idanunta kana cikin raunan'niyar murya tace. “Tabbas baya kashewa ka kira Abbansa kaji”. Kai ya gyaɗa kana yace. “Eh dama zan kirasa amma Innayi tace ko Abbansa ne ya hanasa zuwa ganin hadari”. A hankali tace. “Anya?,Ka kira sa dai”. “Amma yanzu dare baiyi ba Ummi”. Cikin sauri tace. “A'a ka kira Babana ka kira Abbansa ɗin duk yanda kukayi ka kirani ka sanar min”. “Toh”. Moddibo yace kana ya katse kiran. Asma'u da Bashir kuwa zuru-zuru sukayi da ido domin suna iya jiyo sautin muryar Modibbo. Durƙusa wa Asma'u tayi tare da toshe bakinta kana tashiga. Girgiza kanta tare da cewa. “Ya Allah kada ka jarabcemu da abinda baza mu iyaba ɗaukaba Allah ka tsare Yaya Jameel aduk inda yake ya Allah kada ka bari wani abu na cutarwa ya sameshi”. Cikin raunin murya Ummi ta kalleta Atake taji wasu hawaye masu masifar ɗumi sun zubo kuncinta. Ahankali Malam Ahmad da jikinsa yayi masifar sanyi ya ƙarasa kusa da Ummi. Moddibo kuwa yana katse kiran ya shiga contact tare da fito da Number Abban M Jameel. Kana ya Kalli Innayi cikin sanyin murya mai cike da tashin hankali yace. “Kin gani ko Innayi baya can. J baije gidan Ummi ba. Innayi ina J ya tafi bayan yasanar dani cewa zai taho”. Lokaci ɗaya wani masifaffen tsoro da tashin hankali ya ziyarci Innayi wanda ta kasa ɓoyewa har hakan ya bayyana asaman fuskarta dake nuni da tsantsar ruɗu. Cikin dakiya da kuma nuna masa babu komai insha Allah ta gyara tochligt dake hannunta kana tace. “Ka dai kira Abbansa muji wataƙil yana can tare dashi hadarin ne ya hanasa fitowa”. Kai ya gyaɗa mata tare da dearling number Abban M Jameel yana jin yanda zuciyarsa ke cigaba da bugawa da masifar ƙarfi yana bada sautin dif-dumm-dif dumm. Abba dake kwance kan 3sitter Idanunsa arufe bacci ya fara fusgarsa yaji suwwan wayarsa Atsakiyar kansa afirgice ya miƙe tare da zama kana ya duba screen ɗin wayar nan yaga sunan Moddibo na yawo cikin rawan jiki yayi Picking. Atare Abba da Moddibo sukayi Sallama. Ahankali Moddibo ya sauƙe numfashin tare da ƙoƙarin dai-dai-ta nutsuwarsa kana yace. “Wa'alaikum Salam Abba”. Cikin yanayin firgici da ruɗu Abba ya sauƙe ajiyar zuciya tare da cewa. “Na'am Aliyu ya akayi?”. Numfashi Moddibo ya fesar kana yace. “Lafiya Abba”. Kai Abba ya gyaɗa tare da jingina bayansa da jikin kushin kana yace. “Ya gida kowa lafiya dai? Jameelun yaƙara so yana lafiya ko?”. Lokaci ɗaya zuciyar Moddibo ya buga da masifar ƙarfi kana yayi saurin dafe ƙirjinsa tare da cewa. “Abba baya gidane”. Wani irin azabebben bugawa zuciyar Abba yayi kana yace. “A'a bakwa tare ne tun 10:15 ai ya sallameni yace min zai taho wurinka”. Moddibo kuwa da sauri ya rumtse idanunsa tare da dafe jikin step ɗin yana mai jin kansa na masifar sarawa tamkar zai rabe gida biyu cikin raunin murya yace. “Abba tun ƙarfe 10:15 ya fita kuma yace wajena zai zo? Abba tun ɗazu fa nake jiransa ko ƙofar gida bamu rufe ba har yanzu J bai zoba sannan fa nata kiran layukan basa shiga”. Cikin tsananin razani da tsinkewar zuciya Abba ya miƙe tsaye kana yace. “Aliyu mai kace?”. Araunane Moddibo da Idanunsa ke juyawa ya dafe kansa kana cikin sanyin murya yace. “Abba na yita kiran layinsa baya shiga”. A ruɗe Abba ya miƙa tsaye tare da cewa. “Innalillahi wa'inna ilahi rajiu'n to lafiya Aliyu?”. Girgiza kai Moddibo yayi tare da gyara tsayuwar sa kana yace. “Toh Abba kuma yace waje na ɗin zai taho?Abba J bai zoba bafa”. ya ida maganar cikin raunin murya mai cike da tsantsar tashin hankali. Atake zufa ya wanke wa Abba jiki duk da iskar dake kaɗawa d ƙarfi ya haɗiye wani abu mai ɗaci kana yace. “Ko dai gidan Ummin sa yaje”. Da sauri Moddibo ya girgiza kansa muryarsa na rawa yace. “Um-um Abba baya can yanzu nayi waya da Ummi itace ma tace in Kira ka Dan ni Ina tunanin dare ma yayi bazan kira ba”. Cikin tsinkewar zuciya Abba ya nufi ƙofar falon Hajiya Karima da sautin muryansa ya farkar da ita tayi saurin fitowa daga Bedroom ɗin Aruɗe ta kallesa kana tace. “Lafiya Alhj?”. Girgiza kai Abba yayi tare da cewa. “Jameelu ba agansa ba wai baije wajen Moddibo ba sannan baije wajen Umminsa ba”. Da sauri ta dafe ƙirjinta kana tace. “Ba agansa ba kuma gashi yanzu ƙarfe ɗaya”. Kasa cewa komai Abba yayi ya nufi ƙofa da sauri. Tare da cewa. “Miƙo min key mota”. Cikin sauru tabi bayansa tare da Kallonsa ganin Gajeren wando da single ne kaɗai ajikinsa yasa tace. “Toh yanzu ina zaka je adaren nan??”. Cikin raunin murya yace. “Karima ina zanje kike tambaya ta? Jameelu na fa baya gidansu Aliyu sannan baya gidan Umminsa to ina Jameelu yaje kinsan waye Jameelu da in dai baya nan yana gidansu Aliyu ko gidan Umminsa tabbas da akwai abinda yake faruwa”. Cikin sauri ta juya tare da komawa Bedroom ta dauƙa Masa Jallabiya da key mota kana ta sanya hijabinta ta fito tare da miƙa masa. Karba yayi yana tafiya yana saka jallabiyar kana ya nufi inda Motarsa yake ya shiga cikin sassarfa tabi bayansa yana shiga mazaunin Driver itama tayi saurin buɗe gefen mai zaman banza ta Zauna. Kallonta yayi tare da cewa. “A'a ki koma”. Girgiza kai tayi tare da cewa. “A'a Alh ya za'ayi in barka ka tafi kai kaɗai muje dai”. Kai ya gyaɗa batare da yace komai ba ya figi motar. Suka tafi bayan mai gadi ya buɗe masa ahankali ya fara bin hanyar Yana dudduba gefen titin kana cikin sanyin murya yace. “To ko dai motarsa ta samu matsale ne?”. Girgiza kai Hajiya Karima tayi kana tace. “Idan ma motarsa ta samu matsala Alh ai saidai ya kira akawo masa wata”. Kai ya jinjina still Yana cigaba da Driving ɗin yayin da zuciyarsa ke cigaba da bugawa da kaso Cassa'in cikin ɗari suna cikin tafiya har suka isa gidan su Moddibo. Moddibo dake tsaye coumpund ɗin har zuwa lokacin ya gagara koda ƙoƙƙwaran motsi yayi saurin kallon gate ɗin ganin hasken mota Itama Innayi dake tsaye tayi saurin bin wajen da kallo zuciyarta na cigaba da bugawa. Cikin sauri tare da rauni yace. “Toh waye wannan ko dai motar J ne?”. Ya faɗa tare da nufar gate ɗin Innayi kuwa ido ta zuba masa har ya buɗe gate. Moddibo kuwa yana buɗe gate din idanunsa suka sauƙa akan motar Abba. Cikin sauri ya ƙarasa jikin motar tare da cewa. “Abba kaine?”. Jinjina kai Abba yayi asanda ya ƙarasa fita daga motar kana cikin raunin murya yace. “Eh Nine Aliyu ina tsammanin Jameelu yana nan to idan ba nan ba ina Jameelu zai je adaren nan. Amma anya ka bin cika baya gidan Umminsa ba wasa take mana ba?”. Girgiza kai Moddibo yayi cikin mutuwar da jiki da rauni yace. “A'a Abba baya can tunda nayi magana da Ummi kuma yanzu da muka gama waya da kai ma na kirata nace baya can itama kuka fa takeyi”. Cikin ruɗu da rashin sanin madafa Abba yace. “Toh kazo muje can ɗin mu duba may be ko motarsa ta ɓaci ahanya can ya nufa”. Kai Moddibo ya gyaɗa tare da faɗin. “To bari in ɗauki motata dan nasan Innayi ma bazata zauna ita kaɗai agida ba”. Ya faɗa tare da shigewa cikin gida kai tsaye falonsa ya nufa ya ɗauki key sannan suka fito da Innayi acikin motar. Motar Modibbo ce ta shiga gaba na Abba na biye da ita tuƙi kawai Moddibo yake amma baki ɗaya baya cikin nutsuwarsa. Acan gidan Ummi kuwa tunda Moddibo ya sanar mata M Jameel baya gidan Abba hankalinta yayi masifar tashi ta fito coumpund ta tsaya tana kuka yayinda Asma'u da Bashir ke taya ta cikin tsanananin kaɗuwa. Cikin rarrashi da nasiyya Malam Ahmad ke tausanta dasu Asma'u. Cikin sauri Ummi ta ɗaga kanta ganin hasken motoci abakin gate ɗin gidan su. Aruɗe ta kallesa tare da cewa. “Ka kalli hasken mota Malam ko dai Jameelu ne?”. Cikin sanyin murya yace. “Ki kwantar da hankalin ki Fatima dan Allah ki nutsu Insha Allah babu komai, ba abinda zai samu Jameelu”. Kai ta girgiza kana tace. “A'a to ai naga hasken mota ne”. Ajiyar zuciya ya sauƙe tare da riƙe hannunta ganin yanda ta firgice kana yace. “Toh bari naje na duba naga ko waye ne”. Kai ta girgiza kana cikin raunin murya tace. “A'a to muje dai”. Kai ya gyaɗa tare da yin gaba kana tabi bayansa Malam Ahmad na buɗe ƙaramar ƙofa yaga motar Moddibo daf da bakin gate Dai-dai lokacin Moddibo ya buɗe Murfin motar ya fito. Cikin sauri Ummi ta kallesa tare da leƙa motar dake bayansa kana tace. “Babana”. Cikin sanyin murya yace. “Na'am Ummi J bai zo nan ba dagaske?”. Cikin muryan kuka ta girgiza kai kana tace. “A'a bai zo bafa Babana idan yazo ya za ayi in ɓoye muku”. Cikin mutuwar jiki Abba ya buɗe Murfin motar tare da fita kana ya kalli Ummi da hawaye ke bin kuncinta yace. “Fatima”. Saurin Kallonsa Ummi tayi tare da cewa. “Abban Jameel”. Cikin yanayin tashin hankali yace. “Da gaske Jameelu bai zoba?”. Kai ta gyaɗa Masa still Hawaye na bin kun cinta tace. “Bai zoba kuma nata kiran wayoyinsa basa shiga”. Cikintashin hankali da ruɗu suka haɗa baki wajen furta. _“Innalillahi Wa'inna Ilahi rajiu'n Allahumma Ajirni fii musibati wa'ahlifli khairan minha”_. Cikin sanyi Moddibo ya kalli Abba da idanunsa suka sauya launi saboda tashin hankali kana yace. “Abba mu koma ta hanyar gidaku mu duba ko dai motarsa ta samu matsala ne ko kuma yayi hatsari ne?”. Kai suka gyaɗa cikin sauri Ummi ta juya tare da kallon Moddibo kana tace. “Bari na ɗauko hijabina muje tare”. Bata jira jin abinda zasu ce ba ta juya da sauri ta koma tare da ɗaukan hijabinta ta fito coumpund ɗin kallon Asma'u da Bashir tayi wanda har zuwa lokacin suna cikin ruɗani, cikin Muryan kuka tace. “Asma'u ku kula da kanku zamu duba hanya ko Allah zaisa mu gansa”. Cikin sauri Asma'u tace. “Ummi zamu biku”. Girgiza kai Ummi tayi tana tafiya tace. “A'a ku zauna kada ku fito”. Daga haka ta fice Malam Ahmad na ƙoƙarin ɗauko mota Moddibo yace. “Ummi kuzo ku shiga motata kawai”, Kai ta gyaɗa kana tashiga bayan motar kusa da Innayi. Malam Ahmad kuwa a gaba, kana suka fara tafiya koda da irin tunanin da yake Aransa duk wani inda suke tunanin mota zai iya maƙalewa ko kuma hatsari sun duba amma babu M Jameel da motarsa babu dalilinsa har unguwar su Abba suka koma amma still Babu shi babu dalilinsa. Cikin yanayin gajiyawa da ɗimuwa Abba ya buɗe Murfin motar ya fito kana Moddibo da sauran ma duk suka fito. Cikin raunin murya me nuni da razani Abba yace. “Gashi mun biyo har nan ma amma baya nan, to mu gwada zuwa asibiti mu duba ko dai yayi hatsari ne ko yaya”. Cikin raunin murya Moddibo ya Girgiza kai kana yace. “Abba hatsari kuma? Ai da hatsari ne da munga mota kuma da ankira mu”. Kafin Abba yace wani abu Innayi ta kalli Moddibo tare da cewa. “Eh muje dai asibitin saboda Kore shakku”. Jinjina kai sukayi tare da shiga motar kana suka nufi Asibitin. Ahankali Moddibo ya kalli Innayi kana yace. “Toh wani asibitin zamuje kin san dai bawasu manyan asibiti muke dasu ba”. Cikin sanyi malam Ahmad yace. “Mu fara zuwa babban asibitin idan yaso sai mu duba sauran daga baya”. Kai Moddibo ya gyaɗa tare da nufar babban asibitin Abba na biye dasu. Suna isa suka tarar da gate din asibitin arufe kasancewar har biyu tayi,sauran asibitin suka shiga zagayawa amma ko wanne arufe in sun buga an buɗe musuma in sun shiga bashi ba lbrinsa. Cikin han zari Abba ya cewa Moddibo su nufi Private hospital ɗin Abba haka kuwa akayi. Suna isa Moddibo ya sauƙa tare da nufar cikin Hospital kana ya tambayi Norse dake aiki ko M Jameel yazo suka ce a'a juyawa yayi ya shiga motar kana suka ci-gaba da nemansa. Wasa gaske fa babu Jameel ba dililinsa ba motarsa, gaba ɗaya sun shiga ruɗu da zulumi gamida tsoro. Misalin ƙarfe uku hankalin su ya kai ƙololuwa wajen tashi baki ɗaya sun cika da damuwa zuwa wannan lokacin sun tabbatar ba lafiya domin M Jameel baya yawo sannan Gembulan ba wani babban gari ne da keda charking point ba bare su kai report. Moddibo kuwa banda tasbihi da kiran sunan Allah babu abinda yake Aransa yayin da kasala da mutuwar jikinsa ke ƙaruwa fiye da farko kana ga hadarin da zuwa yanzu yayi gangami asama da alamar ruwa na gab da sakƙowa, dan tuni aka fara yayyafi. Abba kuwa tunda suka fito a asibiti ya kifa kansa ajikin motar zuciyarsa na bugawa da masifaffen ƙarfi cikin raunin murya yace. “Acikin wannan daren ga hadari na kira layukan Jameeluna duka basa shiga a wannan yanayin ina Jamilu na ya shiga”. Cikin raunin murya mai cike da karaya Modibbo ya fesar da numfashi mai zafi kana yace. “Yanzu acikin daren nan ina J yake?. Wani hali yake ciki?. Wani irin yanayi yake cikin a wannan daren da kuma hadarin da yake tasowa ina J ɗina yake!?”. Cikin ƙarfin hali Malam Ahmad ya numfasa kana yace. “Insha Allah ba komai mu bari muga zuwa safiya abinda Ubangiji zai yi”. Cikin tsanananin rauni Ummi ta kife kanta da jikin kujeran Motar kana ta fashe da wani Marayan kuka mai gunji”. Cikin damuwa da kuma tausayawa Abba ya juya tare da kallon Malam Ahmad kana yace. “Malam ku tafi gida kaima Moddibo ku koma gida da Innayi kada ruwan nan ya saƙƙo muna nan duk inda ya kamata mu duba mun duba baya nan bari mu gani zuwa safiya”. Girgiza kai Moddibo yayi Araunane yace. “Abba ya za ayi mu koma mu shiga cikin gida mu samu mafaka bayan bamu san halin da J yake ciki ba. Abba ina kake tunanin zamu koma mu samu nutsuwa acikin wannan yanayin bayan bamu san ina J yake ba!?”. Kallonsa Abba yayi cike da rauni yace. “Toh Aliyu ina zamuje mu duba?, Duk inda ya kamata mu duba mun duba sannan wayoyinsa basa shiga wannan shine babban tashin hankalina mu koma gida muyi alwala mu sanar wa Ubangiji halin da muke ciki Aliyu”. Jinjina kai sukayi atare cike da gamsuwa da abinda yace sam tashin hankali da ruɗanin da suke ciki yasa sun kasa samun nutsuwar da zasuyi addu'a. Kai Moddibo ya gyaɗa kana yace. “Toh Abba”. Sannan suka shiga mota Abba yaja ya nufi gidansu cikin tashin hankali da ɗimuwa yayin da Hajiya Karima ke kuka Abba kuwa ko da kallonta ya gagara yi bare kuma ya iya lallashin ta. Ya yinda Moddibo ya nufi gidan Ummi babu abinda ke tashi acikin motar banda sheshsheƙan Kukan Ummi ta rasa shin wani irin tunani zata yi shin ina Jameelunta yake awannan tsohon daren Akuma irin wannan lokacin. Moddibo kuwa cikin tsananin damuwa da zulumi da macewar jiki ya cigaba da Driving har ya isa kofar gidan yayi Parking. Fita Malam Ahmad yayi Ummi ma ta sauƙa suka nufi cikin gidan. Ganin hasken mota yasa Bashir miƙewa da sauri tare da buɗe ƙaramin gate ɗin. Cikin sauri Asma'u da har zuwa lokacin take zaune ta ɗago kanta tare da miƙewa ta riƙe hannun Ummi kana tace. “Ummi Ina Yaya Jameel Ummi kunga Yah Jameel?". Cikin sanyi Ummu ke jujjuya mata kai. Ita kuwa a ɗimauce tace. “Ummi to ina yashiga awannan daren dubi hadari fa wani hali yake ciki?”. Girgiza kai Ummi tayi tare da fashewa da kuka kana tace. “Ban saniba Asma'u Bansan inda Jameelu na yake ba, bansan halin da yake ciki ba Asma'u zuciyata zafi take jinake tamkar kaina zai rabe gida biyu!”. Aruɗe Asma'u tace. _“Innalillahi wa'inna ilahi rajiu'n Allahumma Ajirni fii musibati wa'ahlifli khairan minha_, nashiga uku Yah Jameel”. Cikin sauri Malam Ahmad ya riƙe hannun Asma'u ganin kamar bata hayyacinta kana yace. “Subhanallah Asma'u da iliminki kike kirawa kanki shiga uku kada ki sake haka Addu'a ya kamata mu masa kunji ko?”. Kallonsa ya mayar kan Bashir kana yace. “Kuzo mushiga muyi masa addu'a ayanzu ba kuka Jameelu yake da buƙata daga wajen muba face adduoi”. Kai suka gyaɗa sannan ya sake hannun Asma'u ya riƙe na Ummi Bashir kuma yarike hannun Asma'u suka shiga ciki kai tsaye ko wannensu toilet yashiga ya ɗaura Al'wala kana ya fito suka shimfiɗa Sallaya tare da fara jera nafillah suna roƙon Allah daya fitar da M Jameel aduk halin da yake ciki. Moddibo kuwa suna isa gida yayi Parking tare da rufe ƙofar kana ya wuce falonsa yayin da Innayi ma tashige sashen ta yana shiga kai tsaye toilet dake falon ya shiga ya ɗaura alwala kana ya fito ya shimfida Sallaya cike da nutsuwa ya fara Sallah kana duk sujjadar da zaiyi sai ya roƙi Ubangiji ya kare J ɗin sa aduk inda yake”. Baki ɗaya su haka suka raya wannan daren cike da bautar Ubangiji tare kuma da rokon Allah daya bayyanar da M Jameel kana Allah yaraba sa da duk kan sharrin Mutum da Aljan. Bayan an kira Assalatu Moddibo ya fito ya nufi masallaci ana idar da sallah kai tsaye gidan Abba ya nufa. Yana isa kiran Ummi na shiga wayarsa ciki. Sanyin jiki ya ɗaga wayar tare da kaiwa kunnensa kana yayi Sallama. Cikin dashashshiyar murya Ummi ta amsa Sallamar sa kana tace. “Babana ya labarin Jameelu na?”. Cikin sanyin murya yace. “Ummi nima gashi yanzu nazo wajen Abba naji ko ya dawo gida”. Dai-dai lokacin Abba ya buɗe gate ya fito ganin Moddibo tsaye yasa ya isa wajensa ahankali Moddibo ya zare wayar daga kunnensa bayan yace anjina zai kirata. “Aliyu dama yanzu zanje wajenka”. A hankali Modibbo yace. “Abba to yanzu ya zamuyi”. Numfashi Abba ya fesar tare da cewa. “To mu tafi police station Jiya Baki ɗaya ba muyi tunanin zuwa can ba”. Kai Moddibo ya gyaɗa kana suka shiga motarsa yaja Abba kuwa jingina da jikin kujera yayi baki ɗaya zuciyarsa ta tushe ya rasa wani irin tunani zaiyi yayin da Idanunsa suka tsats-tsafo da ruwan hawaye. Moddibo kuwa Driving yake amma baki ɗaya baya fahimtar komai ko gilmawar mutum ya gani sai yaga kamar J ɗin sane. Suna isa yayi Parking atare suka fito daga motar tare da shiga station din Dpo dake ƙoƙarin fita yayi Murmushi tare da cewa. “Alh Bashiru maidala Barka da zuwa kaine da kan ka?”. Jinjina kai Abba yayi kana cikin sanyin murya yace. “Na kawo report ne ɗana Jameelu ne bamu ganiba”. Cike da mamaki da kuma al'ajabi Dpo da sauran folisawan suka ce. “Ɗan ka Jameelu kuma?”. Kai Abba ya gyaɗa kana yace. “Eh tun jiya ba agansa ba kuma babu motarsa sannan akira layukan sa basa shiga”. Cike da jimami Dpo yace. “Subhanallah Alhj mai yasa baku kawo report tun dare ba!?”. Numfashi Abba ya fesar kana yace. “Yanayin hadari ne sannan baki daya hankalin mu baya Jikin mu sai mukayi tunanin bari muyi addu'a mu kaiwa Ubangiji kukan mu”. Daga nan yayi miki bayanin dukkan abinda ke tafiya. Kai Dpo ya gyaɗa tare da cewa. “Toh shikenan Alhj insha Allah yanzu zamu kira hedquater mu na cikin Taraba afaɗa musu halin da ake ciki”. Kai Abba ya gyaɗa kana yace. “Toh shikenan mun gode”. Moddibo kuwa tun da suka shiga ya jingina da jikin bango Ya Lumshe Idanunsa yana motsa laɓɓansa alamar tasbihi bai ce komai. Wunin wannan ranan baki ɗaya haka gidaje uku sukayi sa cikin zullumi,fargaba da kuma tsantsar tashin hankali Moddibo kuwa duk bayan minti biyu sai ya kira Number M Jameel aƙalla daga Jiya da daddare zuwa yau ya kira wayarsa yafi sau ɗari. Acan ɓangaren Ummi ma haka yakasance bini-bini zata kira layin sa amma amsar ɗaya ake basu shine Switch off. Haka zalika Abba time to time zaiyi try number M Jameel amma akashe Wunin wannan ranan baki ɗaya sunyi zuru-zuru dasu kallo ɗaya zaka musu kasancewa suna cikin tsananin tashin hankali da ɗimuwa duk inda ya kamata su nema ko su bincika duk sun nema sun bincika amman ba lbri. Abba kuwa zama yayi afalonsa tare da kira duk wani danginsa ko kuma abokin arziki ko zaiji Jameelu yaje amma kowa amsa ɗaya yake basa baije ba. Haka zalika Ummi baki ɗaya ta kira danginta ko M Jameel yaje amma suma dai amsar ɗaya ce baije ba. Wunin wannan ranan har dare babu M Jameel babu labarin sa zuwa wannan lokacin tsananin tashin hankali da ruɗun da suke ciki ba zai misaltuba. Da daddare Misalin ƙarfe goma Moddibo ne zaune a falon Abba kansa aƙasa yayinda idanunsa suka kaɗa sukayi ja jawur kana jijiyoyin kansa sun tashi sunyi ruɗu ruɗu rabonsa da bacci tun daren shekaran jiya haka zalika yauma koda runtsawa ne yakasa kana ya sanya duka hannunsa biyu ya dafe kansa dashi zuwa lokacin baki ɗaya ya kasa control ɗin kansa kife kansa yayi ajikin kujera tare da fashewa da kuka mai gunji. Cikin wata raunan'niyar murya mai cike da karkarwa yace. “Abba ina J yake? Abba ina J ya tafi ya barni Abba wani hali J yake ciki?”. Hajiya Karima ce tashigo falon bakinta ɗauke da Sallama tare da kallon Moddibo dake kuka tamkar ƙaramin yaro lumshe Idanunta tayi tare da cewa. “Haba Aliyu kuka kuma kai da ya kamata ka tausashi Mahaifinsa sannan kuma ka zauna zakuyi ta kuka atare kenan?”. Karo na farko kenan arayuwar data yi masa magana cikin taushin lafazi. Ahankali Moddibo ya ɗago kai ya kalleta still yana kuka yace. “Aunty Karima ina J yake Ina J ɗina yashiga ya barni?”. Cikin rauni Abba ya ɗago idanunsa da hawaye ke zuba Akuma dai-dai lokacin wayar Abba ta ɗauki ruri yana ɗagawa yaga number ce ba suna sai ya mayar ya ajiye. Kallonsa Moddibo yayi tare da faɗin. “Abba waye ne?". Ciki Sanyin Abba ya kalli wayar kana yace. “Numbar ce ba suna”. Cikin muryan kuka Moddibo yace. “Toh Abba ka ɗaga mana ko za'a faɗa mana anga J ne”. Cikin sauri Abba yayi Picking call ɗin tare da cewa. “Assalamu Alaikum”. Daga ɗaya ɓangaren cikin wata bauɗaɗɗiyar murya aka amsa da. “Wa'alaikum Salam kaine Alhaji Bashiru Maidala mahaifin Malam Jameelu?”. Cikin sauri Abba ya gyaɗa kai tare da miƙewa tsaye kana yace. “Eh nine mahaifin Jameelu”. Cikin sauri Moddibo ya miƙe tsaye, itama Hajiya Karima cikin sauri ta miƙe tsaye. Gyaran murya yayi kana yace. “Toh Jameelu yana wajen mu”. Cikin rawan baki Abba yace. “Jameelu yana wajen ku yana cikin halin lafiya? To a ina kuke?”. Kai tsaye yace. “Eh gashi ma kaji muryarsa”. Ya faɗa tare da miƙawa M Jameel wayar. Cikin sauri Abba yace. “Jameelu”. M Jameel kuwa cikin wata raunan'niyar murya me cike da galabaita da tashin hankali kamar wanda yayi kuka yana sauƙe ajiyar zuciya yace. “Abbana”. Cikin rawan jiki da rauni Abba yace. “Na'am Jameelu Meye sameka?,Aina kake?”. Ajiyar zuciya mai nauyi M Jameel ya sauƙe cikin rauni da yanayi wahala yace. “Abba nima ban sani ba bansan inda nake ba Abba ina A.J”. Cikin muryan kuka Abba ya kalli Moddibo da jikinsa ke rawa kana yace. “Gashinan". Ahankali M Jameel dake sakin ajiyar zuciya yace. “Abba ka bashi wayar”. Miƙawa Moddibo wayar Abba yayi cikin sauri Moddibo ya amsa tare da mannawa akunnensa kana Yace. “Jyyyyyy”,yaja sunan cike da taraddadi. Fesar da numfashi M Jameel Yayi tare da cewa. “AJ”. Cikin yanayin rauni da tausayawa ya lumshe idanunsa tare da cewa. “J ina kake?”. Girgiza kai M Jameel Yayi kana yace. “AJ ban sani ba bansan inda nake ba, ban san ida suka kawoni ba”. Cikin sauri aka Fisge wayar daga hannun M Jameel kana cikin wannan bauɗaɗɗiyar murya akace. “Ka bawa mahaifinsa waya”. Ahankali kuma cikin sanyi Moddibo yace. “Waye kai ina J yake?”. Cikin wata razananniyar tsawa yace. “Kabawa mahaifinsa waya ba da kai muke son magana ba?". Moddibo kuwa Girgiza kai yayi kana yace. “Toh me kuke so ku faɗa min ko mameye”. Cikin sauri Abba ya janye wayar daga kunnensa tare da sa wayar a handsfree kana yace. “Gani mahaifin Jameelu". Daga ɗaya ɓangaren mutumin yace. “Jameelu yana hannunmu bawai mun sace sa dan mu kashe sa ko wani abu bane amma idan kuka yi mana taurin kai zamu iya kash”... *Littafin SAKAYYAH na kuɗine ƴar uwa 1k ne kacal ki biya ki karanta cikin Aminci ba haƙƙin wani a kanki 0661110170 GTBank AISHA ALIYU GARKUWA. Sai ki turo min shaidar biyanki ta WHATSAPP 09097853276* *By* *GARKUWAR MARUBUTA* [30/07, 1:40 PM] Halimatu A/rahman Sadeeya: *Littafin SAKAYYAH na kuɗine ki biya ki karanta cikin Aminci da salama babu haƙƙin kowa a kanki littafin 1k kacal 0661110170 GTBank AISHA ALIYU GARKUWA sai ki turo min shaidar biyanki ta WHATSAPP 09097853276, sai in saki a Group ɗin* “Idan har kana son rayuwar ɗanka to. Kabi sharaɗin mu kabi tsarinmu, sannan kabi dukkan dokokin, muddin kana so Jameel ya rayu idan kuma ka kuskura kayi mana taurin kai kayi mana gardama kan sharuɗan da muka ginda ya maka to zakaga abinda zai biyo bayan gardama”. Cikin tsanananin kaɗuwa Abba ke girgiza kai yayin da bakinsa ke rawa ya gaza furta komai. Cikin wannan bauɗaɗɗiyar murya mutumin ya cigaba da cewa. “Dama kai tsaye mu aikin kashe sa aka bamu. Toj amma saboda nagartansa da mutuncinsa yasa mukaji bama buƙatar kashe Malam Jameelu munfi ɓuƙatar abada kuɗi musakeshi domin shi Jameelu na kowane, kauda irinsu a doron kasa asarace data shafi, dukkan al'umma, dan haka kabi sharuɗanmu mu sakeshi salamun-salaman ya dawo hannunku hankali kwance, idan kuma ka kuskura kayi mana gardama duk da na gartan Jameel zamuyi abinda muma ranmu bai soba!”. Cikin tsanananin tsoro da tashin hankali Abba ya dafe ƙirjinsa da hannu ɗaya kana yace. “Innalillahi. Dan Allah ku faɗa min koma me kukeso zan baku bazan muku gardama ba da Izinin Ubangiji”. Cikin wata kakkausar murya mutumin yace. “Bayan kai wanda mu kejin sa agefenka kada ya mana gardama domin shine Amininsa Moddibo”. Girgiza kai Abba yayi still jikinsa na rawa kana muryarsa cike da rauni yace. “Ba zaiyi gardama ba”. Gyaran murya Mutumin yayi kana yace. “Kasa amsa kuwwa shima Moddibo yaji abinda ake magana akai”. Kai Abba ya gyaɗa still muryarsa na rawa yace. “Nasa, nasa, nasa”. Cikin bada umarni mutumin yace. “Ku nutsu ku zauna ku jini”. Kai Abba ya gyaɗa kana yace. “Toh”. Gyara murya mutumin yayi cike da isa yace. “Baku zauna ba nasan atsaye kuke”. Atare Abba, Moddibo da Hajiya Karima suka zauna Araunane Abba yace. “Toh mun zauna wallahi”. Kai Mutumin ya gyaɗa tare da faɗin. “Yayi kyau sharaɗin mu na farko da zamu ƙidanya muku idan ka bishi Jameel ya rayu idan kuwa baka bishi ba Jameel ya mutu wannan shine sharaɗi na farko kuma shine mafi tsauri”. Ajiyar zuciya kawai Moddibo ke sauƙewa zuciyarsa na cigaba da bugawa da masifar ƙarfi. Mutumin ya cigaba da cewa. “Sannan yanzu rayuwar Jameel yana hannunka da kai da Amininsa da kuma mahaifiyarsa da ma sauran Makusantan ku, idan kuka mana gardama kamar kuna wasa da rayuwar Jameel ne”. Atare Moddibo da Abba suka haɗa baki wajen cewa. “Meye kuke buƙata menene sharaɗin naku?”. Kai Mutumin ya gyaɗa kana yace. “Sharaɗin namu shine wannan maganar kada ku yarda kada ku kuskura koda agigin bacci koda amafarki kusa hukuma acikinta!”. Moddibo kuwa ƙirjinsa ne ya buga cikin sauri ya dafe kansa da hannunsa biyu tare da kifa fuskarsa ajikin kushin kana ya furta. “Innalillahi wa'inna Ilahi rajiu'n”. Cikin ƙasa da murya Abba ya runtse Idanunsa tare da cewa. “Innalillahi wa'inna ilahi rajiu'n La'ilaha Illah anta subhanaka Inni kuntu Minal Zhalimin”. Cikin tsawa mutumin yace. “Zaku faɗa kenan!?”. Da sauri Moddibo ya girgiza masa kai dake kife akan kushin kamar yana gabansa kana yace. “Ba zamu faɗa ba wa kowa ba, mudai fatan mu J ya kasance cikin ƙoshin lafiya, kada ku cutar dashi”. Taɓe baki Mutumin yayi kana yace. “Kada ku yarda kada ku kuskura ku sanya hukuma aciki”. Ajiyar zuciya Abba ya sauƙe tare da fesar da numfashi kana yace. “Ba zamu faɗa ba da izinin Ubangiji zamu bi sharaɗin ku. Amma sai dai kafin ma ku kiramu mun kaiwa hukuma maganar amatsayin Jameel ya ɓata tunda mun kwana babu shi sannan mun wuni babu shi toh munje wajen hukuma amma bawai munje amatsayin mun kai ƙorafi akan ku bane”. Jinjina kai Mutumin yayi tare da taɓe baki kana yace. “Toh wannan sharaɗine Idan hukuma sun dawo dan suna nan kamar Mayu, daga sunji babu mutum idan sun sake kawo kansu kada kuce mun nemi kuɗi awajenku”. Yarfe hannu Hajiya Karima tayi tare da girgiza kai ta ƙurawa Abba Ido tamkar shike maganar. Cikin bauɗaɗɗiyar murya Mutumin ya cigaba da cewa. “Muddin kana son ran Jameel to. Kayi shiru da bakin ka idan mun kafa maka sharaɗi na biyu ko kuma mun faɗi abinda mukeso kun bayar to Jameel zai dawo amatsayin ɓata yayi sannan ba sace sa akayi ya dawo ba”. Abba kuwa buɗe idanunsa dake lumshe yayi kana yace. “Insha Allah zamu bi sharaɗin ku amma yanzu mai kuke so ku faɗa min”. Cikin sauri ya janyo wayar tare da kallon screen ɗin jin ɗit-ɗit-ɗit alamar an kashe. Ajiyar zuciya Abba ya sauƙe tare da rintse idanunsa da karfi kana yace. “Innalilahi wa'inna ilahi rajiu'n Hasbunallahu wani'imal wakin”. Moddibo kuwa da still hannunsa ke dafe akansa yana taune lip ɗin sa na ƙasa babu abinda ke fita abakinsa face kalmar Innalillahi wa'inna ilahi rajiu'n. Hajiya Karima kuwa Girgiza kai kawai take tare da yarfe hannu kana tana mai maimaita kalmar Hasbunallahu wani'imal wakin ta juya tare da kallon Abba da idanunsa suka kaɗa suka yi jawur sannan tace. “Innalillahi wa'inna Ilahi rajiu'n wannan wani irin zamani Allah ya kawo mu kenan ƴan Kidnapping ne suka ɗauke Jameelu”. Lokaci ɗaya Moddibo ya sake dafe kansa da karfin yana cigaba da taune lip ɗin sa na ƙasa. Girgiza kai Hajiya Karima tayi kana ta cigaba da cewa. “Amma Alhj wannan sharaɗin nasu zancene na banza ina muke da yaƙinin zasu iya kare Jameelu ba zasu cutar da shiba ba gwara mu faɗawa hukuma ta shiga cikin maganar nan ba”. Cikin sauri Moddibo ya ɗago kansa daga jikin kushin wanda sai alokacin ya samu damar hakan hannunsa biyu ya haɗe waje ɗaya alamun roƙo kana ya runtse Idanunsa da ƙarfi ya shiga. Girgiza kansa muryarsa na rawa yace. “A'a,a'a,a'a Aunty Karima kiyi wa Allah da Manzonsa kada ki sako hukuma acikin maganar nan Wallahi kina sa hukuma zasu iya yiwa J komai kiyiwa Allah kada kisa hukuma aciki kiji abinda suka faɗa mana”. Abba kuwa jujjuya kai ya shiga yi kana idanunsa akan Hajiya Karima yace. “Karima ban yarda ba ban yafe ba wannan maganar ya fita muddin kinaso Jameelu na ya dawo kada ki faɗawa hukuma wannan maganar”. Kai ta gyaɗa cike da damuwa. Kallon wayarsa Abba yayi tare da cewa. “Yanzu bari na sake kiransu naji me suke buƙata”. Ya faɗa tare da dearling number amma swich off”. Ɗagowa Abba yayi tare da kallon Moddibo kana yace. “Aliyu Wayar akashe”. Cikin sauri Hajiya Karima tace. “Ai dama zaiyi wuya yashiga ya za ayi ya shiga ai ba zai taɓa shiga ba”. Daga Abba har Moddibo babu wanda yace komai Allah ne kaɗai yasan abinda suke ji aransu. Dai-dai lokacin Hajiya Turai ta shigo bakinta ɗauke da Sallama kusa da Hajiya Karima ta zauna Idanunta sun kaɗa sunyi jawur har sun kumbura alamar tayi kuka ta gaji Idanunta akan Abba tace. “Alhj har yanzu babu labarin Jameelu”. Kafin Abba yace wani abu Hajiya Karima tayi saurin cewa. “Yan zun nan ƴan Kidnapping sun Kira su suka ɗauke sa!”. Cikin sauri Hajiya Turai ta dafe ƙirjinta tare da cewa. “Hasbunallahu wa niimal wakil Innalillahi wa'inna ilahi rajiu'n,Ƴan Kidnapping kuma Alhj!?”. Girgiza kai Abba yayi sai kuma ya riƙe tafin hannunta kana yace. “Ki zauna”. Ba musu ta tazauna jikinta na rawa saboda tashin hankali da take ciki. Ajiyar zuciya Abba ya sauƙe kana ya maida kallonsa kan Hajiya Karima tare da cewa. “Wannan maganar daga mu sai mu iya mu nan kada ku kuskura maganar nan ta fita iya mu nan ban amince ba kuma ban yafe ba daga ke har Karima ban amince ku kai maganar nan kunnen hukuma ba, duk wacce takai abakin igiyoyin auren ta duka saboda sun sa sharaɗin idan na yarda hukuma ta shiga zasu kashe min Jameelu”. Ya ida maganar cikin raunin murya. Kai Hajiya Turai ta girgiza cikin Muryan kuka tace. “Innalillahi wa'inna ilahi rajiu'n in sha Allah ba zamu faɗa ba Alhj yama za ayi mu faɗa ai wannan ba abin faɗa bane!”. Hajiya Karima ma cikin sauri ta girgiza kai kana tace. “Insha Allah ba zamu faɗa ba, zamu kiyaye”. Moddibo kuwa har zuwa yanzu yana dafe da kansa da hannu biyu still Idanunsa aruntse. Ahankali Abba ya kira sunan sa tare da cewa. “Aliyu”. Araunane Moddibo ya ɗago idanunsa da sukayi Jawur kana sun kumbura ga lip ɗin sa na ƙasa sunyi ja kana ya ɗan kumbura. Cikin rauni ya kalli Abba tare da cewa. “Na'am Abba”. Ajiyar zuciya Abba ya sauƙe kana yace. “Aliyu ya zamuyi?”. Zazzafafar ajiyar zuciya Moddibo ya sauƙe tare da cewa. “Abba sai dai mu jira kiran su na biyu muji mai suke buƙata magana ce dai na kuɗi atanadi abinda suke bukata a ajiye tun wuri”. Kai Abba ya gyaɗa tare da cewa. “Toh Aliyu amma yanzu ya zamuyi da mahaifiyarsa inaga kada ka faɗa mata halin da ake ciki”. Moddibo kuwa kallon Abba yayi kana ya girgiza kansa tare da cewa. “Abba kar afaɗa mata kuma? Ai gwara tasan cewa J yana raye, domin zuciyar Ummi zata iya bugawa da idan ba afaɗa mata ba gwara in Faɗa mata tasan cewa J yana raye tasan cewa munyi magana da shi naji muryansa, kaima kaji muryan J fa yanda muka yi magana dashi ƙilan sun dake shi!”. Ya faɗa cikin raunin murya. Runtse Idanu Abba yayi da ƙarfi hawaye masu zafin gaske suka shiga bin kuncinsa Shar-shar-shar. Moddibo kuwa still Idanunsa na runtse ya gagara buɗewa har zuwa yanzu yana jin muryan M Jameel na cewa A.J bansan inda nake ba ban san ina nake ba. Cikin rauni ya ɗago kansa muryarsa na rawa yace. “Abba kaji fa J cewa yake baisan inda yake ba Abba ina suka kaisa ina suka cusa sa”. Dafa kansa Abba yayi kana yace. “Aliyu duk yanda za ayi idan ka faɗawa Fatima kada ta faɗawa kowa, sannan ka kiyaye yanda zaka faɗa mata kada hankalinta ya tashi!”. Girgiza kai Moddibo yayi kana yace. “Abba ba zata faɗawa kowa ba idan na faɗa mata halin da ake ciki”. Jinjina kai Abba yayi tare da cewa. “Toh shikenan Aliyu ka kula”. Kai Moddibo ya gyaɗa dai-dai lokacin kiran Ummi ya shigo wayar Moddibo kallon Abba yayi kana yace. “Abba ka gani ko kirana ma take yi yanzu kafin na wuce gida ma saina biya wajenta”. Cike da rauni Abba yace. “Toh shikenan tashi kaje Aliyu gashi kaima har ƙarfe goma na dare yayi tsoro nakeji, jiya a irin ya wannan lokacin suka ɗauki Jameelu”. Runtse Idanu Moddibo yayi tare da miƙewa kana ya yiwa su Hajiya Turai sallama ya fita har kofar gida Abba ya rakasa sai da yaga tashin motarsa kafin ya koma cikin gida zuciyarsa na zafi. Cikin sanyin jiki yayi parking kana ya fita ƙaramin ƙofar ya tura ya shiga A baranda ya hango Ummi, Asma'u da Bashir Idanun Ummi da Asma'u sun kaɗa sunyi Jawur dasu kana sun kumbura. Bashir kuwa cikin dauriya kasancewar sa namiji yasa ya riƙe hannun Asma'u dake kuka tare da cewa. “Ummi ki kwantar da hankalin ki da izinin Ubangiji ba abinda zai samu Yah Jameel Allah zai tsaresa aduk inda yake Asmey ki daina kuka dan Allah”. Girgiza kai Asma'u tayi cikin Muryan kuka tace. “Bashir taya zamu iya tsaida hawayen mu bayan bamu san halin da Yah Jameel ke ciki ba!?”. Cikin rauni Ummi ta ɗago kanta Idanunta ya sauƙa akan Moddibo dake shigowa Iska na kaɗa sa duk yayi sauya cikin sauri Ummi ta miƙe jikinta na rawa ta nufesa tare da cewa. “Babana”. Ajiyar zuciya ya sauƙe tare da fesar da numfashi kana ya zuba mata Ido cike da tausayawa ganin kamar bata cikin nutsuwarta ƙarasawa kusa da ita yayi tare riƙe hannunta kana suka zauna agefen barandar cikin sanyin yace. “Ummi”. Kallonsa tayi tare da cewa. “Na'am Babana ya labarin Jameelu na”. Sunkuyar da kansa yayi tare da cije labɓansa na ƙasa wanda zuwa lokacin sunyi masifar ja kana sun kumbura yayin da Idanunsa ke tsats-tsafo da ruwan hawaye sai dai sun gagara zubo wa. Ahankali ya ɗago kansa tare da damƙe hannun Ummi na dama acikin nasa kana yace. “Ummi munyi waya da J”. Cikin sauri Ummi ta zaro Idanunta duka waje kana tace. “Kayi waya da Jameelu”. Kai ya gyaɗa mata hawaye masu zafi suka zubo akuncinsa. Kallonsa Ummi tayi tare da faɗin. “Kayi waya da Jameelu Babana kuma kana kuka!?”. Moddibo kuwa kallonta yayi cikin ƙoƙarin tsaida hawayen sa yace. “Ummi anyi Garkuwa Da shine”. Cikin matsanancin tashin hankali Asma'u ta ɗaura hannunta akai tare da cewa. “Innalillahi wa'inna ilahi rajiu'n”. Ta dire addu'ar tare da komawa ta zaun. Ita kuwa Ummu wani irin zazzafan numfashi ta fesar tare runtse idanu kana ta buɗe su akan Moddibo cikin dan sassaucin tashin hankali da take ciki tace. “Toh ai ba komai Babana kawai Abbansa yayi ƙoƙarin haɗa kuɗi da suke buƙata a basu, su sako mana shi. Alhamdulillah tunda yana raye, domin ai wannan abune da ya zama ruwan dare, tunda su dai in an basu abinda suke so basa kisa.” Sai kuma ta lumshe idanunta wasu sirran hawaye suka gangaro mata cikin raunatacciyar murya tace. “Waya sace min Jameelu na!? Waya sacemin farin ciki na!? Waya ɗauke min jin daɗina!? Waya ɗauke min Garkuwana da gatana!? Wayake son yimin shamaƙi da bangona majinginata!?”. Moddibo kuwa hannunta ya riƙe acikin nasa kana yace. “Ummi dan Allah ki daina kuka addu'a zakiyi masa kamar yadda kikace abinda suke so kawai za'ayi musu, sun kuma gargaɗemu kada asa hukuma a cikin mgnar, sai muyi ƙoƙarin kiyayewa”. Kai Ummi ta gyaɗa tare da share hawayen ta amma still wasu na zubowa. Ajiyar zuciya Moddibo ya sauƙe tare da zayyane mata duk yanda sukayi. Atare Asma'u, Ummi,da Bashir suka sauƙe nannauyan numfashi. Kallon Moddibo Ummi tayi kana tace. “Babana basu faɗi nawa suke so bane?”. Kai ya girgiza tare da cewa. “Ummi basu faɗa ba tukunna sharaɗin su na farko suka bamu kada ayarda a faɗawa hukuma”. Ajiyar zuciya mai haɗe da jan zuciya Ummi ta sauƙe still tana hawaye tace. “Ba zan faɗa ba Insha Allah bazan faɗa ba Babana. Ba zan faɗa ba”. Kai Moddibo ya gyaɗa tare da cewa. “Ummi ki cigaba da addu'a Insha Allah babu abinda ya gagari Ubangiji kuma Insha Allah tunda suka fara kira zasu sake kira su faɗi abinda suke so sai ayi ƙoƙari amusu abinda suke so”. Jinjina kai tayi kana tace. “Insha Allah gobe zanje gidan su muyi magana da Abbansa idan Malam ya bari”. Dai-dai lokacin Malam Ahmad ya shigo cike da tausayawa yake Kallonsu kana yace. “Nama bari Fatima na bari Allah ya tsaresa ya kuma bayyana sa aduk inda yake”. Atare suka amsa da Ameen. Miƙewa Moddibo yayi kana yace. “Ummi zan tafi gida”. Kai ta gyaɗa kana tace. “Toh Babana Allah ya kiyaye”. Ameen ya amsa sannan ya juya ya fice cikin mutuwar jiki. Yana isa gida yayi Parking tare da fitowa ya rufe ƙofar kana ya shiga falon baki ɗaya abubuwan sun ca kuɗe masa ga rashin bacci rabonsa da bacci tun daren shekaran jiya ga tashin hankali da damuwa baki ɗaya zulumi sun mishi rubdugu ya fita hayyacinsa sai alokacin ya tuna baki ɗaya wayewar garin yau baiyi wanka ba cikin kasala ya nufi toilet din sai dai baya tunanin zai iya yin wanka, al'wala ya ɗaura kana ya fito tare da shimfiɗa darduma ya fuskanci alƙibla cike da nutsuwa ya shiga gabatar da nafillah aduk lokacin da ya kai goshinsa kasa (Sujjada)Sai ambaci J dinsa, raka'a huɗu yayi bayan ya idar ya ɗauki Alkur'ani mai girma kana ya fara karantawa Acikin Suratul An-Nisa'i har Misalin ƙarfe 2:00am yana karatun idan ya karanta wani aya sai M Jameel ya faɗo Masa arai kana ya tuna da wasu lokutan idan yana karatu yazo wajen Ayar azaba saiya rufe Kur'anin ya Rungume kana yaita kuka idan kuma yazo wajen Ayar Rahma sai yaita sakin murmushi kana yana cigaba da karatun. Ahankali Moddibo ya runtse Idanunsa tare da Rungume Kur'anin aƙirjinsa idanunsa sun kaɗa sunyi jawur dasu kana sun kumbura saboda tashin hankali da yake ciki har aka kira Assalatu Moddibo bai rintsa ba. Haka zalika ɓangaren Abba ma ya kwana ba tare daya rintsa ba acikin kwana ɗaya da yini duk ya canza yayi zuru-zuru dashi. Washe gari da safe:Misalin ƙarfe 8:00am Abba ne zaune afalonsa ya ƙurawa wayoyinsa Idanu koda motsin kirki ya gagara baki daya hankalin sa nakan wayarsa. Cike da ladabi mai gadi yayi Sallama ɗagowa Abba yayi ya kallesa kana ya amsa masa Sallamar. Cike da tausayawa mai gadin yace. “Alhj ga baƙi awaje”. Numfashi Abba ya fesar kana yace. “Su waye ne?”. Tsayuwa mai gadin ya gyara kana yace. “Hukumar ƴan sanda ne wai daga Taraba suka zo”. Kai Abba ya gyaɗa tare da cewa. “Toh ka shigo dasu”. Kai mai gadin ya gyaɗa kana ya fice yace su shiga. Dai-dai lokacin Moddibo yazo Parking motarsa Yayi kusan atare suka shiga ƴan sandan mutum biyar na gaba shi Kuma yana bayansu. Bakinsu ɗauke da Sallama suka shiga wajen zama Abba ya nuna musu bayan ya amsa Sallamar su. Moddibo kuwa gefensa ya nufa ya zauna cikin mutuwar jiki da damuwa. Gyaran murya ɗaya daga cikin ƴan sanda yayi kana Idanunsa akan Abba yace. “Sunana Asp Mahmud Adam Shani daga rundunar ƴan sandan jahan Taraba masu bincike akan abinda ya shafi ɓatan mutane da kuma kisan kai kana da fashi da makami ina fatan zaku bamu haɗin kai. Mun samu kirane daga nan ƙaramin Headquarter din mu”,'. Sai kuma ya sauƙe numfashi tare da kallon Moddibo da yayi ƙasa da kansa kana yana motsa laɓɓansa alamar tasbihi yake. Kana ya cigaba da cewa. “Mun samu masaniya Kan cewa Jameel ɗan Alhj Bashiru Maidala ya ɓata shiyasa nazo da kaina inji ba'asin maganar sannan muga ta inda ya kamata mu fara da taimakon Allah da kuma baya nan da zaku bamu zamuyi nasara wajen gano inda yake”. Jinjina kai Abba yayi tare da rintse idanunsa kana ya fesar da numfashi tare da sunkuyar da kansa ƙasa hawaye masu zafi suka zubo masa. Cike da tausayawa Asp Mahmud Adam Shani yace. “Alhj ka kwantar da hankalin ka kayi min duk kan bayanin da zan gane saboda yanda zamu kula da aikin da kuma abinda ya kamata ayi akai”. Jinjina kai Abba yayi tare da ƙoƙarin hana hawayensa zuba kana ya daure yace. “Jameelu nine mutum na ƙarshe da yayi sallama dani ya fita ina tsaye ajikin window har ya fita bayan fitarsa na kai kimanin awa ɗaya da rabi ina tsaye ajikin window, Bayan nan kuma duk cikin mu babu wanda yayi magana da Jameelu domin ya fita akan zaije wajen Abokinsa amma bai isa ba”. A hankali ya fesar da zazzafan iska tare da taune lip ɗin sa na ƙasa tare da kallon Asp Mahmud Adam Shani kana yace. “Adaren Abokinsa yazo domin rashin samun layinsa da bai yiba”. Jinjina kai Asp Yayi kana yace. “Eh anyi min wannan bayanin daga Headquarter din mu na Nan Inspector Ayuba Garba kumo ya sanar dani komai to amma daga ɓatansa zuwa yanzu babu wanda ya kira ka!?”. Cikin sauri Abba ya Girgiza masa kai kana yace. “A'a babu". Ido Asp ya zuba masa kana yace. “A'a Alhj Bashir dan Allah kada kuce zaku bi sharuddan ire-iren mutane masu garkuwa da mutane, idan har akwai wanda ya kira ka ya maka barazana ko kuma ya nemi wani abu ka faɗa mana ko kuma ka bami number da suka kira Insha Allahu Jameelu zai kuɓuta sannan zai rayu da izinin Ubangiji zamu tsera tar dashi”. Moddibo kuwa cikin sauri ya kalli Asp zuciyarsa na bugawa da masifar ƙarfi ya Girgiza kai tare da cewa. “Babu wanda ya kira ai da akwai wanda ya kira zamu sanar daku sannan mu ma da hankalin mu zaifi kwanciya ma, mun san cewa yana raye”. Ido Asp ya tsira musu kana yace. “Anya kuwa anya babu wanda ya kira ku!?”. Cikin sauri Moddibo ya gyaɗa kai kana cikin ƙoƙarin dai-dai-ta nutsuwarsa yace. “Babu wanda ya kira tashin hankalin mu kenan”. Abba ya karɓi maganar da cewa. “Da har ankira Asp Mahmud da ace ankira kamar yanda kake zaton ƴan Kidnapping ne kuma sun buƙaci kuɗin ai da tuntuni nayi muku bayani sannan idan yakama da in basu kuɗi zasu dawo min da Jameelu na da tuni na bayar an dawo min da Jameelu na!”. Anutse Asp ya gyara zamansa kana cikin sauri yace. “Alhj na roƙe ka dan Allah koda ankira ance kuɗi ake buƙata kada ka basu, kawai ka bamu Number sannan kayi mana bayani shine abinda muke bukata amma ana temakamu sune sannan ana ƙara basu ƙarfin gwiwa dayi musu abinda suke so shiyasa suke ƙara yin abinda suke su ɗin”. Ajiyar zuciya Abba ya sauƙe tare da jingina bayansa da jikin kujeran kana yace. “Insha Allahu zanyi ƙoƙari duk abinda ake ciki zan sanar muku Nagode sosai musamman tattakin da kayi daga Taraba zuwa nan”. Dai-dai lokacin Hajiya Karima tazo Idanunta akan Asp Mahmud Adam Shani da sauran Folisawan Kallonta ta mayar kan Abba kana tace. “A baƙi mukayi ne sannun ku da zuwa”. Asp dake rubutu awata ƙaramar takarda yace. “Yawwa”. Kana ya cigaba da rubuce-rubucen sa. Kallon Abba Hajiya Karima tayi tare da kallon Moddibo da idanunsa ke lumshe haƙoransa uku na sama na kan laɓɓansa na ƙasa numfashi ta fesar kana ta ƙara sa kusa da Abba da har zuwa lokacin bayansa ke jingine ajikin kujera tace. “Alh ga Hajiya Fatima mahaifiyar Jameel ta iso”. Ahankali Abba ya ɗago kansa kana cikin sanyin murya yace. “Kice ta iso”. Kai ta gyaɗa tare da juyawa ta fita ba jimawa ta shigo Ummi na biye da ita Ahankali Ummi ta ƙara sa kusa da Moddibo ta zauna Hajiya Karima ta juya ta fice cike da tausayawa Moddibo da Abba ke kallonta ganin yanda Idanunta suka kumbura sukayi jawur sun ƙanƙance. Anutse Asp ya ɗago kansa tare da kallon Ummi kana yace. “Wannan ce mahaifiyarsa?”. Kai Abba ya gyaɗa tare da faɗin. “Eh itace”. Atausashe Asp ya gyara zamansa tare da cewa. “Sannu Mmn Jameel Ubangiji Allah ya bayyana sa ya kuma tsaresa aduk inda yake, ki kwantar da hankalinki in sha Allah zamuyi iyakar iyawarmu zamu samoshi a duk inda yake”. Kai ta gyaɗa cikin muryanta daya dishe da kuka tace. “Ameen ya Allah”. Miƙewa Asp Yayi kana yace. “Alhj to bari mu tafi amma dan Allah duk abinda ake ciki a faɗa mana”. Kai Abba ya jinjina tare da cewa. “Toh Insha Allah”. Bayan tafiyarsu Ummi ta juya tare da kallon Abba cikin raunin murya tace. “Alhj har yanzu basu sake kira ba!?”. Kai Abba ya gyaɗa kana yace. “Fatima har yanzu basu kira ba”. A raunace ta sanya gefen hijabinta tare da share hawayen da suka zubo mata kana tace. “To idan sun sake kira duk abinda suke so dan girman Allah kataima keni kaceci rayuwar Jameel kayi musu”. Girgiza kai Abba yayi idanunsa na tara ƙwalla yace. “Fatima ba sai kin roƙeni kin haɗa Ni da Allah ba, idan har banyi musu abinda suke so andawo min da Jameel ba menene amfanin dukiyata?”. Sai kuma ya runtse Idanunsa kana ya cigaba da cewa. “Jameel yafi min komai aduniyar nan zan iya sadaukar da duk dukiyata domin ceton rayuwar Jameel insha Allah zanyi iya bakin ƙoƙarina wajen ganin ya dawo”. Ajiyar zuciya ta sauƙe kana tace. “Toh shikenan Nagode Ubangiji Allah ya kuɓutar dashi Allah yasa su faɗi abu mai sauƙi kada su faɗi abinda yafi ƙarfin mu Allah ya tsaresa Allah yasa yana cikin ƙoshin lafiya”. Atare Moddibo da Abba ke Amsawa da Ameen cike da tausayawa. Kallon Abba tayi kana tace. “Bari na tafi gida”. Kai Abba ya gyaɗa kana yace. “Toh shikenan”. Cikin sanyin murya Moddibo yace. “Ummi muje in kaiki gida”. Kai ta gyaɗa kana ta miƙe. Suka fita da kallo Abba ya bisu cike da tausayawa. Moddibo kuwa yana ajiye Ummi agida kai tsaye makarantar Malam Arɗo ya nufa yana isa yayi Parking tare da fita ya nufi harabar makarantar iska na kaɗa shi kai tsaye Office din malam Arɗo ya Murɗa handle din ya shiga bakinsa ɗauke da Sallama. Anutse Malam Arɗo dake duba wani littafi ya ɗago kansa tare da sauƙe Idanunsa akan Moddibo ganinsa cikin wani irin yanayi yasa yayi saurin miƙewa tare da riƙe hannun sa kana yace. “Moddibo ya dai?”. Kai Moddibo ya Girgiza cikin sanyin murya yace. “Bakomai”. Kujera Malam Arɗo yaja masa ya zauna kana shima ya koma mazauninsa. Cike da kulawa Malam Arɗo yace. “To ina ƴan biyun naka?”. ƙasa yayi da kansa tare da runtse Idanunsa kasancewar sa ba mai saurin kuka ba ya tabbata da ace yana da saurin kuka da zaran an ambaci sunan J ɗin sa zaiyi kuka ko hakan zaisa ya samu sassaucin abinda yake ji Aransa ya sake damƙe lip ɗin sa da ƙarfi wanda zuwa lokacin ya sake kumbura kana yayi ja sai sheƙi yake. Ido Malam Arɗo ya tsira masa kana yace. “Ya dai Aliyu mai yake faruwa da Jameelu tun jiya da yamma naji ana raɗe-raɗin wai ba agansa ba nayi ta kiran wayarka baka ɗauka sannan shi kuma idan na kirasa akashe ina Jameelu da gaske ne babu shi!??”. Ajiyar zuciya ya sauƙe tare da ɗago kansa still yana taune da lip ɗinsa kana cikin raunin murya yace. “Babu J”. Kai Malam Arɗo ya gyaɗa kana yace. “Na sani Aliyu ka nutsu ka dawo hayyacinka Aliyu na sani babu Jameelu sannan na gaskata tunda har naga kai kaɗai kazo nan na tabbata do min idan anganka tamkar anga wata ne dole za'aga zara”. Ya faɗa tare da miƙewa ya dafa kafaɗar sa. Runtse Idanu Moddibo yayi “Yanzu ya ake ciki?”. Ajiyar zuciya Moddibo ya sauƙe tare da shafa ƙirjinsa dake bugawa da ƙarfi kana yace. “Nima kaina ya kulle a duniya bansan me zanyi ba bansan ya zanyi na ganni da J ba?”. Dafa kafaɗar sa Malam Arɗo yayi cike da tausayawa yace. “Toh yanzu wani mataki aka ɗauka akan lamarin!?”. Cikin raunin murya yace. “Babban matakin da aka ɗauka shine addu'a da faɗawa Ubangiji abinda yake faruwa”. Jinjina kai Malam Arɗo yayi tare da faɗin. “An ɗauki mataki mai kyau, da girma wanda ya dace da dukkan Musulmi yanzu mu shiga cikin makaranta mu faɗawa yara su tayamu da addu'a Ubangiji Allah ya tsare malam Jameelu ya kuma bayyana sa aduk inda yake”. Kai Moddibo ya gyaɗa tare da miƙewa kana yace. “Toh Nagode Allah ya saka da alkhairi”. Hannunsa Malam Arɗo ya riƙe bayan ya mike suka fita kai tsaye bangaren ƴan primary suka fara shiga Ajinsu Ramadan da Raudat yaran na ganinsa suka miƙe cike da farin ciki suna cewa Moddibo Moddibo Kusan a tare Raudat Ramadan da wasu ɗalibai uku suka ce Moddibo ina Malam Jameel munyi kewar ku bakwa zuwa. Lumshe Idanunsa da yaji suna masa zafi da zaran an ambaci sunan J ɗin sa zuciyarsa zata buga da masifar ƙarfi tsayuwar sa ya gyara agaban ajin tare da cewa. “Ina ɗaliban Malam Jameel?”. Baki ɗaya yaran suka ɗaga hannu suna tsalle tare da cewa gamu nan Moddibo ina yake munyi kewarsa bakwa zuwa yanzu, dan Allah kace yazo muna san ganinsa. Kasa furta komai Moddibo yayi hakan yasa ya jingina bayansa da jikin bango yayi ƙasa da kansa yasan yanda J ɗin sa ke son Yara da kuma wasa da su wanda a ra'ayinsa baison koyar da yara amma saboda yanda J ɗin sa ke son Yara Yasa yake shiga koyar musu ganin haka yasa Malam Arɗo yayi gyaran murya Atake duk yaran suka nutsu tare da tsirawa Malam Arɗo ido. A hankali Malam Arɗo ya sauƙe tare da faɗin. “Kuna jina?”. Kai suka gyaɗa masa. Ya sauƙe numfashi tare da cewa. “To zaku yiwa Malam Jameel din ku addu'a Allah ya bayyana shi?”. Aruɗe yaran suka ce Malam Jameel ya ɓata ne?." Kai Modibbo ya gyaɗa musu cike da damuwa. Cikin zare ido Raudat tace. “Malam Jameel din mu ya ɓata kuma to ina yaje?”. Ramadan kuwa miƙewa yayi tare da zuwa gaban blackboard ɗin cikin yanayin damuwa sosai ya riƙe hannun Moddibo da har zuwa lokacin Idanunsa ke lumshe yace. “Moddibo ina Malam Jameel ɗin mu yaje dan Allah ka kira wayansa kace ya dawo Muna so sa”. Kasa cewa komai Moddibo yayi sabida zulumi. Gyaran murya Malam Arɗo yayi tare da cewa. “Kuyi masa addu'a Allah ya bayyana shi idan kunyi sallah kuyi addu'a Allah ya bayyana Malam Jameel sannan ku faɗawa iyayenku suma suyi masa addu'a Allah ya karesa ya kuma dawo dashi cikin aminci da salama”. Hawaye Ramadan ya fara zubdawa tare da cewa. “Toh Malam zamuyi masa addu'a zan faɗawa Mommy da Addah Khausina suma zasuyi masa addu'a Allah zai dawo dashi”. Ahankali Moddibo ya shafa kansa tare da cewa. “Yawwa Ramadan kuyi masa addu'a ayanzu babu abinda Malam Jameel yake buƙata awajen mu face addu'a” Cikin rauni sosai yaran suka ce zamu yi masa. Cikin sanyin jiki Malam Arɗo da Moddibo suka fita zuwa bangaren Secondary bayan sun fita anan suka shiga ɓangaren na naziri saida suka gama zagaye ko wani aji suna sanarwa Ayiwa Malam Jameel addu'a Ubangiji Allah ya bayyana shi cikin tashin hankali ɗalibai suka shiga masa addu'a. Bayan sun fito Moddibo ya nufi hanyar gate Cikin kula malam Arɗo yace. “Moddibo baza ka shiga office din ku ba?”. Kai ya girgiza tare da cewa. “Um-um bazan shiga ba zan tafi bazan iya zama babu J ba”. Ya faɗa tare da ficewa yashiga motarsa kai tsaye gidan Abban M Jameel ya nufa bayan yayi Parking ya fito tare da shiga falon bakinsa ɗauke da Sallama A inda ya fita yabar Abba anan ya dawo ya sameshi zaune still wayarsa na gabansa ya zubanusu Ido da alama tun bayan fitarsa ko motsawa baiyi ba. Ahankali Abba ya ɗago kai tare da zuba masa ido cike da tausayinsa baki ɗaya ya rame ya canza idanunsa sun sake girma da ja kana idanunsa sun faɗa, Ahankali Moddibo ya ƙaraso ya zauna agefensa aƙasan Capet Cike da tausayawa Abba yace. “Aliyu ba kayi wanka ka sauya kaya ba”. Siririn tsaki Moddibo yaja tare da yin ƙasa da kansa kana yace. “Abba har yanzu basu sake kira ba!?”. Kai Abba ya Girgiza tare da cewa. “Har yanzu basu sake kira ba gani nan ina zaune tamkar gadin waya nake sai tsumayin kiransu nake amma basu kira ba, amma yanzu ka samu kaje kayi wanka ka samu kaci abinci”. “Abba banajin yuwa”. “Ya zamuyi Aliyu idan kaima baka ci abinci ba ai faduwa zakayi. Insha Allah addu'ar mu bazai bar Jameelu ya ta gayyara ba”. Sai ya kuma maida kallonsa kan Hajiya Karima data shigo wacce ita ma baki ɗaya tayi sanyi ahankali yace. “Ki zubawa Aliyu sbinci”. Kai ta gyaɗa tare da nufar dining ta ɗauki Plate ta zuba masa jollof fice da yaji bushesh-shen kifi da namar kaza ta kawo masa. Moddibo kuwa hannu ya daga mata alamar kada ta ajiye masa ganin ta ajiye yasa ya maida kansa jikin kushin ɗin ya jingina tare da lumshe idanunsa yace. “Ina ma ace tare suka ɗauke Ni da J da yafi min farin ciki ina rayu dashi aduk inda yake duk halin da yake ciki ace muna tare wallahi da yafi min farin ciki akan rabani da Jameel da sukayi”. Kallonsa Abba yayi cike da tausayawa wannan shine karo na farko arayuwar sa da yaji Moddibo ya kira Complete sunan M Jameel cikin raunin murya yace. “Toh ya zamuyi Aliyu ka daure kaci abinci”. “Abba ba zan iya cin abinci ba”. Cikin rarrashi Abba yace. “Haba Aliyu ka naso kasake sa kamu cikin damuwa ne rashin cin abinka dai dai yake da yiwa kan ka illah, wanda bazan so hakan ba dan Allah ka daure kasa wani abu acikin ka”. Kai Moddibo ya gyaɗa kana yace. “Toh Abba abani tea”. Miƙewa Hajiya Karima tayi ta nufi dining kana ta haɗa masa tea cup ɗaya ta kawo masa ahankali ya karba tare da kaiwa bakinsa da ƙyar ya iya shan rabi ya ajiye Cup ɗin. Abba bai tilasta shiba dan shima akaran kansa yasan ba zai iya saka komai acikin sa ba baya ga tea ɗin da yake sha dan raya kai, cikin sanyin murya yace. “Aliyu kaje ɗakin Jameelu kayi wanka ka sauya kaya”. Girgiza kai yayi cikin rawan murya yace. “Abba bari in je gida saboda nabar Innayi ita kaɗai tun safe sannan na barta cikin damuwa”. Kai Abba ya gyaɗa tare da cewa. “Toh Aliyu ka gaisheta”. Yana isa gida yayi Parking tare da wucewa Bedroom ɗin sa, kai tsaye toilet ya shiga tare da sakarwa kansa ruwan sanyi sai alokacin ya lura da Dick ɗin sa daya kwanta luƙui tamkar bai taɓa tashi ba tsanananin fargaba da tashin hankali da yake ciki yasa ya kasa tantance shin shi ɗin wani irin halitta ko kuma wanne irin jinsi ne shin shi ɗin namiji ne ko mace baisan matsayin da yake ba bare kuma ace sha'awa baki daya Dick ɗin sa ya kwanta tamkar babu wani abu mai suna sha'awa daya taɓa ji cikin sanyi Jiki ya gama wankan tare da fitowa ya shirya cikin Jallabiya kana ya fesa turare kai tsaye sashen Innayi ya nufa. Misalin ƙarfe 5:00pm da wasu Mintuna bayan antaso Amakaranta motarsu Ramadan na shiga harabar gidan tayi Parking Ramadan ya ɓude tare da ficewa da gudu. Acan falo kuwa Mommy da Khausar ce zaune suna kallon TV cikin tashar Nat geo well Suna kallon namomin daji Ramadan ya shigo tare da zama gefen Khausar kana ya langwaɓar da kansa tare da cewa. “Addah Khausi”. Hankalinta na kan wasu irin halittun ruwa tace. “Na'am Ramadan”. Cikin muryan rauni yace. “Addah Khausi wai Malam Jameel ya ɓata”. Cikin sauri ta kallesa tare da riƙe hannunsa kana cike da mamaki tace. “Malam Jameel ya ɓata kuma!?”. Kai ya gyaɗa mata kana yace. “Eh Addah Khausi Moddibo da Malam Arɗo su suka shiga ajinmu suka faɗa mana Malam Jameel ya ɓata ba asan inda yake ba”. Cike da mamaki da kuma al'ajabi Khausar tace. “Ha'a wace iriyar magana ce wannan Malam Jameel ya ɓata ba'a san inda yake ba!?”. Mommy kuwa cike da mamaki take kallon Ramadan kana tace. “Ramadan ka tabbatar kuwa?”. Kafin yace wani abu Raudat ta shigo da kuka fuskarta jage-jage da hawaye kana ta zauna kusa da Mommy tare da cewa. “Wallahi Mommy wai ya ɓata!”. Da sauri Mommy ta ɗauki wayarta dake hannun kujera kana tace. “Gashi kiramin Umminsa”. Amsar wayar Khausar tayi still da mamaki atare da ita tace. “Eyyy aikuwa Jiya naga miss call ɗin Asma'u bana wajen daga baya kuma da nazo ina ta kiranta bata ɗaga ba”. Dai-dai lokacin Hajiya Bunayya ta shigo sanye da hijabi har ƙasa kana ta zauna kusa da Khausar dake laluɓo number Ummi ya zama na sun sa Ramadan Atsakiya kasancewar kujeran 2sitter ne. Bayan Mommy ta amsa Sallamar ta tace. “Hajiya wai kinji abinda yaran nan suke faɗa wai Malam Jameel ya ɓata!”. Kai Hajiya Bunayya ta gyaɗa tare da cewa. “Eh dama baki ji bane aini tun jiya da yamma Aminu ke faɗa min wai yaji Amasallaci ana cewa ayi addu'a Allah ya bayyana ya kuma tsaresa ashe dama ba kiji ba?”. Kai Mommy ta. Girgiza fuska cike da damuwa tace. “Innalillahi wa'inna ilahi rajiu'n Wallahi ban jiba Subhanallah ya Salam Ubangiji Allah ya tsaresa”. Hajiya Bunayya kuwa ahankali ta saci kallon Mommy sai taga idanunta nakan Khausar data maƙala waya akunnenta cike da dabara ta sake murza turaren dake hannunta kana ta fito dashi ta ɗaura akan Ramadan tana shafa masa aranta kuwa fari fess tana cewa Alhamdulillah wannan turaren dai na samu na shafa masa saura kuma gobe in faɗawa Boka Kar'uzu na shafa masa turaren. Khausar kuwa jin Asma'u tayi Picking call ɗin yasa cikin sauri tace. “Asma'u”. Cikin wata dashash-shiyar murya mai cike da rauni Asma'u tace. “Na'am Khausar”. Cikin alamun damuwa Khausar tace. “Asma'u wai me nake ji?”. Cikin muryan kuka Asma'u tace. “Khausar an sace Yah Jameel yau kwana biyu kenan kusan na uku ba Yaya Jameel ba labarinsa”. Atsorace Khausar ta dafe hannunta aƙirji kana tace. “Innalillahi wa'inna ilahi rajiu'n ansace Yah Jameel Kuma?”. Kai Asma'u ta gyaɗa hawaye na bin kuncinta tace. “Eh”, Cikin sanyin murya tace. “Ubangiji Allah ya bayyana shi aduk inda yake Allah ya fito mana dashi”. Ameen Asma'u ta amsa tare da katse kiran. Kallon Mommy Khausar cikin tashin hankali tace. “Mommy wallahi da gaske an sace sa”. Girgiza kai Mommy tayi tare da cewa. “Ya Salam wallahi bamu sani ba barin idan Abbanku ya shigo zan tambaye sa muje muyi wa Umminsa jaje Ubangiji Allah ya bayyana shi Allah ya tsaresa aduk inda yake”. Khausar kuwa kasa tsaida hawayen ta tayi cikin Muryan kuka tace. “Ameen Mommy Ameen ya hayyu ya ƙayyum Allah ya bayyana Malam Jameel har kwana biyu kuma!?”. Ta gumi Hajiya Bunayya tayi tare da marairaice fuska kana tace. “Hakane kam wannan duniyar ta zama abin tsoro idan kana fama da talauci ka banu idan kayi wadata ɓarayi da ƴan Kidnapping su hanaka kwanciyar hankali da nutsuwa Allah dai ya kyauta”. Ta faɗa tare da miƙewa ta fice ranta fess. Baki ɗaya Wunin wannan ranan haka Mommy da Khausar suka yita cikin jimami da fargaba musamman Khausar ta gagara tsaida hawayen ta. Moddibo kuwa yana fita daga sashen Innayi mota ya shiga tare da nufar gidan Abba yana isa ana kiran maghariba tare da Abba suka shiga Masallaci suka gabatar da sallah. Acan ɓangaren Mommy kuwa bayan an idar da sallar Isha'i ta sanarwa da Lamiɗo suna san zuwa yiwa Ummi jaje nan yace ba damuwa ta kira Khausar da Hajiya Bunayya su fito bayan sun fito da kansa yayi Driving ɗinsu zuwa gidan Ummi. Bayan sun isa. Mommy ce agaba sai Khausar sai kuma Hajiya Bunayya bakinsa ɗauke da Sallama suka shiga dai-dai lokacin kuma maƙotansu suka fito. Zaune suka samu Ummi kan 2sitter tana riƙe da Kur'ani Idanunta sun kumbura sun ƙanƙance yayin da Asma'u ke zaune gefenta hannunta riƙe da Carbi. Cikin sauri Khausar ta ƙarasa kusa da Asma'u tare da riƙe hannun ta kana tace. “Asma'u da gaske wai dagaske ansace Yah Jameel!?”. Cikin zubda hawaye Asma'u ta gyaɗa mata kai kana tace. “Khausar da gaske ansace Yah Jameel tun randa kikazo ya maida kin nan, har yanzu babu labarin sa yanzu kusan dare na uku kenan za ashiga”. Khausar ma cikin zubda hawaye ta damƙe hannun Asma'u tare da cewa. “Innalillahi wa'inna ilahi rajiu'n”. Kallon Ummi Hajiya Bunayya tayi tare da cewa. “Ayyah Ummin Jameel Ashe abinda ya faru kenan toh Ubangiji Allah ya tsare Allah ya bayyana shi”. Kai Ummi ta gyaɗa tare da faɗin. “Ameen ya Allah Nagode”. Mommy kuwa kafaɗar ta ta dafa kana tace. “Ba komai Ummin Jameel kiyi haƙuri ki daina kukan nan ki riƙa yi masa addu'a Insha Allah Ubangijin zai bayyana shi”. Cikin sauri Ummi ta share hawayenta kana tace. “Nagode Mommyn Khausar Nagode³”. Cike da tausayawa Mommy ke sake ƙarfafa mata guiwa. Ahankali Khausar ta juya tare da kallon Ummi cikin Muryan kuka tace. “Ummi Allah ya bayyanar da Yah Jameel insha Allah ba zasu samu nasarar cutar da shiba zamu tayi masa addu'a Allah ya karesa”. Miƙewa Hajiya Bunayya tayi kana tace. “Bari mutafi Alhj na jiran mu awaje yace a gaidaki". Kai Ummi ta gyaɗa tare da cewa. “Nogeda Allah ya saka”. Sannan suka fita a coumpund suka haɗu da wasu matan sun shigo yiwa Ummi jaje bayan sun koma gida. Baki ɗaya Khausar ta kasa nutsuwa kafin ta kwanta taje tayi alwala kana ta ɗauki Kur'ani tana ta karatu tare da tawassali dashi da niyyan Ubangiji ya bayyana M Jameel aduk inda yake. Misalin ƙarfe goma na dare kamar lokacin da aka dauke M Jameel Moddibo dake gefen Abba ya miƙe da niyyar tafiya Akuma dai-dai lokacin wayar Abba dake gabansa ta hau ruri. Atare Abba da Moddibo suka kalli wayar cikin sauri Abba yayi Picking call ɗin tare da kaiwa Kunnensa. Daga ɗaya ɓangaren akace Alhj Bashiru mahaifin Jameel ko!?”. Cikin sauri Abba ya gyaɗa kai tare da cewa. “Eh nine nayi ta kiran layinku baya shiga”. Cikin fusatacciyar murya Mutumin yace. “Dama ce maka mukayi idan ka kira zai shiga?”. Girgiza kai Abba yayi tare da faɗin. “A'a to menene sharaɗin ku na biyu kaga ban faɗawa kowa ba!”. Cikin bauɗaɗɗiyar murya Mutumin yace. “Kuɗin fansa zaka biya shine sharaɗin mu na biyu”. Kai Abba ya gyaɗa tare da cewa. “To nawa kuke buƙata?”. Kai tsaye mutumin yace. “Milion ɗari biyu”. Atsorace Abba ya dafe hannunsa aƙirji kana ya zare ido cikin tsanananin firgici yace. “Milion ɗari biyu!?”. Atare Hajiya Bunayya da Moddibo da maganar ya dakesu suka haɗa baki atare wajen cewa. “Milion ɗari biyu?”. Cike da gadara Mutumin yace. “Toh idan ba zaka bada ba sai ka shirya karɓan gawar ɗan ka!”. Cikin sauri Abba ya Girgiza kai tare da cewa. “Kuyi hakuri dan Allah dan darajar Annabi kada ku kashe wayar”. Cikin Yanayin ɓacin rai Mutumin yace. “To ai mun riga mun faɗa muku abinda ake buƙata idan ka shirya gobe zamu sake kiran ka muji ko ka shirya”. Yana gama fadar haka ya katse kiran...! By *GARKUWAR MARUBUTA* [30/07, 1:40 PM] Halimatu A/rahman Sadeeya: *Littafin SAKAYYAH dai na kuɗi ne ba free book bane 1k ne kacal ki biya ki karanta cikin Aminci kada ki karanta na sata na Allah ya isa. 0661110179 GTBank AISHA ALIYU GARKUWA sai ki turo min shaidar biyanki ta WHATSAPP 09097853276 sai in saki a Group ɗina* Cappande. Acikin tafin hannunsa ya ɗebo sulallan Gwal ɗin da wasu yan guntu-guntun sanduna tare da birbiɗin yashin kana ya shiga jujjuyasu, ahankali ya maida kallonsa kan Innayi data gyaɗa masa kai alamar ya fito dasu hannunsa ya zura acikin tukunyar yashiga kalato salullan wanda na ainihin Gwalne aƙalla sun kai guda ashirin, karkaɗe yashin yayi tare da fitowa dasu kana ya ɗaura su akan rigarsa tare da gyara zaman sa abakin ramin ya tsura mata Ido Innayi ma ido ta zuba masa ganin yanda ya zauna yasa tashiga maida yashin ta rufe ramin kana ta sanya duwatsun ta rufe tare da tura fantekar kan ramin kallon Moddibo dake binta da kallo tayi kana tace. “Ɗaura min randan nan akai”. Ajiyar zuciya Moddibo ya sauƙe still Idanunsa na Kanta cikin sanyin murya yace. “Innayi wannan kamar Gwal?”. Kai ta gyaɗa masa kana tace. “Eh Gwal ne” Still ba tare daya motsa ba ya sake kallon Gwal ɗin kana yace. “Ina kika same su Innayi?”. Girgiza masa kai tayi kana tace. “Wannan ba lokacin tambayar ina nasamu gwala-gwalai bane. Moddibo lokacine daya kamata ace ka lissafa su muga adadin su kana musan nawa za'a samu mu haɗa mu karɓo Jameelu yanzu tashi mubar wajen nan mushiga ɗaki kaga dare ya tsala”. Kai ya gyaɗa mata tare da cewa. “Toh”,Kana yabi bayanta tare da tsira mata idanu cike da ɗumbin mamaki tare da tarin tuhuma ahankali ya sake kallon sulallan Gwal ɗin dake haɗe da waɗanan sanduna guntaye aciki asaman laɓɓansa yayi sallama tare da shiga ɗaki. Wutan ɗakin Innayi ta kunna Atake haske ya zagaye ɗakin bayan Moddibo ta ratsa tare da rufe kofar ɗakin kana ta dawo kusa dashi ta tsaya tare da sanya hannunta ta tsistsince ƴan guntulayen sandar ta shiga haɗawa kasancewar akwai wajen haɗawa ajiki Moddibo kuwa Idanu ya zuba mata cike da mamaki. tana cigaba da haɗawa ga mamakinsa sai yaga ya zama sanda irin wanda manyan Limamai ke riƙe wa suna tafiya dashi sanda ce mai masifar kyau da tsari wacce da ka gani kasan mai tsadace. Kallonsa Innayi tayi tare da cewa. “Wannan sanda ce samansa inda ake riƙewa ne kaɗai keda Gwal sai kuma ƙasan sa inda ake dogara wa amma wannan bazan baka shiba saboda ba zaiyi daraja sosai ba. Saboda ahaɗe yake da sanda kana sandar kuma bazan siyar ba, sulallan dai zaka haɗa ka duba sai dai sunzo mana alokacin da bashine ba saboda sulallan baki ɗaya sun ƙare”. Ido kawai Moddibo ya zuba mata still da shock atare dashi. Innayi ta cigaba da cewa. “Baki ɗaya nauyin karatunka. Cin mu, shan mu, suturar mu, tun kana ƙarami da duk wani abinda ya kama su nake ɗauka in siyarwa Alhaji Hashim mai sayan gwala-gwalai shiyasan farashin sulallan duk yanda suke zan faɗa masa adadin da suke yazo ya siya muyi lissafi muga nawa za'a samu”. Kai Moddibo ya gyaɗa tare da cewa. “Toh shikenan”.Yayi mgnar tare da lumshe idanunsa, baki ɗaya damuwarsa asamu kuɗin bawai tunaninsa ya tambayi ina tasamu gwala-gwalan nan ba sannan bashida kuzarin da zai iya tambayar ta, sandar na menene, kana bashi da ƙarfin zuciyar jin mai yasa baza asayar da sandar ba, ayanzu burinsa bai wuce asamu ahaɗa kuɗaɗen akarɓo J ba. Ajiyar zuciya ya sauƙe tare da kallon Innayi kana yace. “Toh zan tafi dasu ɗakina”. Kai ta gyaɗa masa kana ya miƙe ya fita yana jin confidence da farin ciki yasan Gwal nada daraja duk da cewa ƴan ƙananun sulallane amma yasan da izinin Ubangiji zasuyi daraja. Acan gidan Abba kuwa bayan tafiyar Moddibo Hajiya Karima ta kalli Abba daya zurfafa acikin tunani kana ta ɗan ya mutse Fuska tace. “Alhji wai yanzu baza ka sake ƙara neman ragi ba? yanzu sai ka ɗauki Million ɗari da hamsin ka basu mai kake tunanin zai faru gaba idan sunji daɗi za'a sake ɗaukan ƴaƴanka ne fa!”. Anutse Abba ya ɗago kansa tare da kallonta kana cikin sanyin Murya yace. “Karima to me kike tunani?”. Ba yabo ba fallasa tace. “Ka nemi ragi”. furzar da iska mai zafi yayi still Idanunsa na kanta kana yace. “Karima kamar baki ji me yace ba, cewa fa yayi muddin aka nemi ragi akan rayuwar Jameel”. Cikin sauri tace. “Bafa za'a kashe Jameel ba, kawai Alhj idan zaka nemi ragi ka nemi ragi, sai kace baka sha zafin neman kuɗin ba zaka ɗauka agabtale ka basu kamar ba kasan darajar suba, amma babu yanda zaka ɗauki wannan maƙudan kuɗin ka bayar akan Jameelu!”. Cike da mamaki Abba ya kalleta kana cikin ɗaga sautin murya yace. “Karima to idan ban bada kuɗi akan Jameelu ba akan wa kike so in bayar? Shin Karima anya Karima?”. Wani irin kallo ta masa kana cikin sauri tace. “Anya me?”. Dai-dai lokacin Hajiya Turai ta shigo baki ɗaya ta hargitse babu walwala afuskarta ta kalli Hajiya Karima kana tace. “Ai dai kam abin nata da mamaki, idan bai ɗauki kuɗi ya bayar akan Jameelu ba akan wa kike so ya bayar?”. Sai kuma ta maida kallonta kan Abba da idanunsa ke lumshe kana tace. “Aini Alhj naga ƙoƙarin ku ma da har kuka iya neman ragin da suka rage muku, kuma ai sunyi ƙoƙari ni dai anawa tunanin kada ku kuskura kada ku sake yin batun ragin wasu kuɗin, suje su kashe mana yaro abanza idan aka kashesa mai son sa keda asara wanda bai sonsa kuma bai damu ba”. Ta ida maganar hawaye na ciko kwarmin Idanunta. Hajiya Karima kuwa wani kallo ta watsa wa Hajiya Turai tare da cewa. “To mekike nufi?”. Taɓe baki Hajiya Turai tayi kana tace. “To ai gaskiya ne duk mai son Jameelu ba zai so ace za'a sake neman ragi ba”. Taɓe baki Hajiya Karima tayi tare da watsa mata kallon banza kana tace. “Kenan kina nufin Ni bana son Jameelu?”. Hannu Hajiya Turai ta buɗe kana tace. “A'a wannan ke ki kafaɗa da bakin ki amma dai shawaran da kika kawo ba shawara me kyau bace”. Hannu Abba ya ɗaga musu tare da kallon Hajiya Karima dake kumfar baki kana yace. “Bana son hayaniya ya isheku. Dan Allah kubarni inji da abinda ke damuna”. Kai Hajiya Turai ta gyaɗa tare da tsuke bakinta alamun itama ba hayaniyar take soba. Cikin sanyi ta kalli Abba tare da cewa. “Alhj ga Million biyu a Account ɗina zan bayar ahaɗa”. Wani shegen kallo Hajiya Karima tabi Hajiya Turai dashi kana cikin taɓe baki tace. “Hmmm munafurci dai da neman gindin zama haddasu kaza acikin cin danƙo”. Cikin sanyi Abba yace. “Nagode Turai Allah ya saka da alkhairi ayanzu kyauta koda na Naira biyar aka bani ita ina buƙatar ta, xansa acikin tumunin kudin da za'a karɓo Jameel”. Cikin sauri Hajiya Karima tace. “Nima Allah ya bani in bayar”. Kai ya gyaɗa kana yace. “Ameen”. Juyawa tayi ta fice Hajiya Turai kuma ta zauna gefensa tana sake tausansa. Acikin kwanaki biyu Moddibo ya saida gwala-gwalan da kuma motocinsa dana M Jameel Yayi total ɗin kuɗin sun kama Million ashirin da biyar ya turawa Abba cikin account ɗin sa Alhamdulillah yanzu akwai Million casa'in da biyar acikin account ɗin Abba Aɓangaren Abban ma yana cigaba da fafutuka ganin ya samu kuɗi. Acikin kwanakin baki ɗaya abubuwa sun kankama baki ɗaya sun sake maida hankalinsu kan neman kuɗin suga sun samu sun haɗa yau ya kama kwanan M Jameel goma kenan awajen Kidnappers din kana yau kwana biyu rabon Abba da Moddibo suyi waya da M Jameel Misalin huɗu na yamma Moddibo ya bar gidan Abba ya nufi gidansu bayan sun sake tattauna wa. Acan ɓangaren Boka Kar'uzu kuwa Hajiya Bunayya da Hajiya Lami ce gurfane agabansa cikin wata sandararriyar murya Boka Kar'uzu ya kece da wata mahaukaciyar dariya tare da jujjuya gashin dake wangamemen tafi hannunsa kana ya ɗago kansa tare da Kallon Hajiya Bunayya da jajayen Idanunsa da suka tara kwantsa yace. “Kin tabbatar gashin yaron ne dai ko?”. Cike da ƙwarin gwiwa Hajiya Bunayya ta jinjina masa kai tare da faɗin. “Tabbas na tabbatar Boka Kar'uzu Uban bokaye La'anannen Uban La'anannu Mugu Uban mugaye tsinanne Uban tsinannun wannan gashin kan Ramadan ne domin dana shafa turare na shafa kansa bayan na fita naga gashi ya manne ahannu shine na tattare na kawo maka kamar yadda ka umarceni. Wata mahaukaciyar dariya. Boka Kar'uzu ya sheƙe dashi wanda yasa bukkan da suke ciki ya hau girgiza cike da jin daɗin kirarin data masa yace. “Hhhhh magana ta ƙare Ƙaramar la'ananniya me kafirar zuciya aiki ya riga yayi anwuce babinsa saura na Babban”. Girgiza kai Hajiya Bunayya tayi tare da cewa. “Agama da batun Ramadan ɗin kafin ayi na Haiydar to babu matsala wannan ba damuwa bace”. Ajiyar zuciya Hajiya Lami ta sauƙe kana tace. “Ni kuma Boka yanzu Abban Samira na nan amma nanda sati biyu masu zuwa zai tafi aikin Umrah, shiyasa nayi shiru da batun zuwan Samira nan mu bari sai mahaifinta ya tafi kaga ba kowa agida da banaso daga gidan Hajiya Bunayya arika zuwa ana daukan ta saboda sa idanawa. Amma Alhj na tafiya idan ya kama ma ta dawo gidan ka idan kuma kaine ma zaka rinƙa kwana idan gari ya waye ka dawo to duk daya”. Wata dariya mai masifar ƙara Boka Kar'uzu ya kece dashi kana buga ƙafarsa na hagu wanda baki daya ƙura ta buke wajen kana yace. “Hhhhh saishi Boka Kar'uzu Uban bokaye La'anannen Uban La'anannu Mugu Uban mugaye tsinanne Uban tsinannun shaiɗani Uban shaiɗanu babu wata matsala da zaran ya tafi zan zo Ni da kaina dan zamu fi sakewa agidan naku acan ma zan tare in ragargaji sabon budurci”. Kai Hajiya Lami ta gyaɗa tana murmushi kana tace. “Yanda kake so haka za'ayi”. Daga nan suka miƙe suka fita ta baya kamar yanda suka shigo suka nufi gida ransu fari soll musamman Hajiya Bunayya. Acan ɓangaren Khausar kuwa sanye ta fito cikin hijabi maroon mai facemaks kafadarta rataye da jaka fari sol jikinta na fitar da sanyayyan ƙamshin turaren Oud Ma'aruf cikin yanayin sanyin ta da tun ɓatan M Jameel bata dawo dai-dai ba ta kalli Mommy dake zaune kan 2sitter kana tace. “Mommy zan tafi”. Kai Mommy ta gyaɗa kana tace. “To kice ina gaida Ummi”. Kai Khausar ta gyaɗa cike da nutsuwa ta fita tare da sanya Platshoe fari Anutse ta nufi coumpund ɗin dai-dai lokacin da Amina da Uncle Naseer suka shigo hannunsu sarƙafe da juna kallo ɗaya Khausar ta musu ta kawar da kanta gefe kana ta lumshe Idanunta. Ido Uncle Naseer ya zuba mata tare da shafa kansa kana cikin sakin fuska yace. “A'a Khausi ina zuwa da yamma nan?”. Batare data sake kallon inda suke ba kana cikin sanyin murya tace. “Zanje gidan su Asma'u ne”. Langwaɓar da kai yayi kana yace. “Ai haka dai maganar bata haɗa muba Khausar, ashe wai Malam Jameel aka sace Agaskiya garin nan ya fara bada tsoro bari muje na kaiki in jajantawa Ummi”. Girgiza kai Khausar tayi kana tace. “A'a kabari kawai”. Cikin sauri Amina ta watsawa Khausar harara kana ta maida kallonta kan Uncle Naseer Shima ta hararesa. Uncle Naseer kuwa ganin kallon da Amina ke jifansu dashi yasa ya ware idonsa tare da sakar mata da lallausan murmushi kana yace. “Ohh Baby Colm down mu nayin Auren mu zan ɗauke ki mu gudu mubar ƙasar nan, kafin muma Akinnafemu tunda kinga anfara tsincr ƴaƴan masu kuɗi an ɗauke Malam Jameel next target ɗin su ni za'a ce za'a saɓe ko ke, kafin ma su ankara zamu gudu abinmu. Dariya Amina ta ƙyalƙyale dashi tare da manna kanta ajikin damtsen hannunsa. Khausar kuwa cikin sauri ta kawar da kanta gefe tare da lumshe Idanunta. Ahankali Uncle Naseer ya ɗago kansa tare da tsura wa Khausar Ido tabbas soyayyanta acikin jininsa yake har yau har gobe zuciyarsa na muradin Khausar, itace burinsa Kawai zai Auri Amina ne domin cikar Burinsa amma Khausar itace muradinsa. fesar da iska mai sanyi yayi yana jin wani irin yanayi agame da ita kana yace. “Khausi jirani in ɗauko sakon Uwaniyona inzo in kaiki?”. Da sauri Amina ta janye kanta dake manne adantsensa kana tace. “Ka kaita kuma?”. Kai ya gyaɗa tare da yimata raɗa akunne yace. “Yes My dear wife ai jaje ne". Ashagwaɓe ta girgiza kai tare da cewa. “Gaskiya Ni dai Uncle Naseer bana so ka tafi ka barni”. Shafa fuskarta yayi kana yace. “Bafa daɗewa zanyi ba”. Khausar kuwa cike da takaicin abinda sukeyi tace. “A'a Uncle Naseer ka bari ganan Haiydar ma zai kaini da mashin ɗinsa”. Kai ya gyaɗa still Idanunsa na kanta yace. “Ok”. Dai-dai lokacin Haiydar ya fito daga sashen Abbansu hannunsa riƙe da key mashin dinsa. Kallon Uncle Naseer da Haiydar yayi da murmushi afuskarsa yace. “Uncle Naseer yau dai Addah Khausy ta yarda in jata amashin ɗina”. Cikin alamun so Naseer yace. “To ayi a hankali dai banda fifita”. Dariya Haiydar yayi tare da cewa. “Uhmm aikam zata sha fifita”. Murmushi Uncle Naseer yayi tare da cewa. “Dan Allah ka jata ahankali kada kayi mana asara”. lumshe Idanunta tayi baki ɗaya bata da wani kuzari ɓatan M Jameel yayi masifar ratsata hakan yasa ko magana bata fiye yiba daga Um-sai Um-um. Haiydar kuwa mashin ya ɗauko tare da ɗaukar ta suka fice kana Amina da Uncle Naseer suka shiga ciki. Haiydar na isa kofar gidan Ummi yayi Parking ahankali Khausar ta sauƙa tana gyara zaman hijabinta kana atare suka shiga cikin Falon Ummi bakinsu ɗauke da Sallama. Ummi dake zaune riƙe da carbi ahannunta Asma'u da Bashir na zaune gefenta suka Amsa Sallamar. Cike da ladabi Haiydar ya gaisheta tare da sake yi mata jaje kana suka gaisa da Bashir tukunna suka fice atare. Khausar kuwa cike da sanyin tace. “Ummi ki kwantar da hankalin ki insha Allah yaya Jameel zai bayyana babu abinda zai sameshi da izinin Ubangiji addu'a mu bazai tafi abanza ba". Jinjina kai Ummi tayi cikin yanayinta kamar mara lafiya tace. “Ameen ya Allah”. Cikin sanyin murya Asma'u da Muryanta ya dishe da kuka tace. “Babbar matsalar mu yau kwana biyu kenan Basu sake kira ba gashi baki ɗaya kuɗin Million Casa'in da biyar aka samu aka haɗa”. Kallonta Khausar tayi tana cire hijabinta tace. “Haka dai kika cemin jiya har yanzu kuɗin basu haɗuba”. Kai Asma'u ta gyaɗa mata kana tace. “Basu haɗu ba Khausar damuwar dake damunmu kenan wlh, baki ɗaya hankalinmu ya kasa kwanciya sai dai Yah Modibbo yace Abba ya nemi bashin banki amman sunce yau ko gobe zai samu kuɗin”. Cikin sanyin murya Khausar tace. “Insha Allah kuɗin zasu haɗu da izinin Ubangiji Allah ya karesa ya tsare lafiyarsa”. Atare suka amsa da Ameen. Shiru Khausar tayi tare da tallafe kuncinta kana ta kalli Ummi da Asma'u sai kuma ta fesar da numfashi kana buɗe jakarta tare da kwaso ƴan kunnaye da sarƙa da kuma zobe kala biyu da alamun nata dana Mommy ne, hannun Ummi ta kama tasasu a ciki kana ta rufe hannun Ummin tare da cewa. “Gashi inji Mommy na, tace Dan girman Allah da Manzonsa kada ki ƙi karba Ummi dan Allah kada kice komai a saidashi a haɗa kuɗin. Cikin tsananin jin dadi Ummi ta kalli girman Gwal ɗin musamman na Mommy wanda a ƙalla shi kadai zai iya kai one Million da yan ɗori. Hawaye na tsiyayo mata tace. “Bazan ƙiba Khausar kicewa Mommynki ngd matuƙa ubanji yayi mata sakayya da gidan al'janna mai girma”. Cikin sanyi duk suka amsa da Amin. Cikin sanyi Khausar ta fesar da numfashin kana a hankali tace. “Amma Ummi Meyesa ba asa Police acikin maganar ba?”. Cikin raunin murya Ummi tace. “Sunce muddin Akasa police acikin maganar to abakin ransa”. Cikin sauri ta dafe ƙirjinta tare da cewa. “Innalillahi akan ransa kuma?”. Kai Asma'u ta gyaɗa Tare da cewa. “Kuma batun kuɗi ma da suka ce da farko Million ɗari biyu sukace yanzu ya zama Million ɗari da hamsin saboda ragin da aka nema to yanzu sunce muddin aka sake neman ragi akan ransa”. Aruɗe Khausar ta rintse Idanunta tare da cewa. “Innalillahi wa'inna ilahi rajiu'n”. Sai kuma ta juya tare da kallon Ummi cikin sanyin murya tace. “Ummi kinsan wani abu?”. Kai Ummi ta girgiza kana tace. “A'a”. Lumshe idanu Khausar tayi tare da cewa. “Ummi ranan da Yah Jameel ya mai dani gida da muna tafiya munga wata mota tana ta binmu abaya”. Sai kuma tayi shiru alamar tunani ajiyar zuciya ta sauƙe kana tace. “Ummi shine fa dama nace da za'a faɗawa hukuma zan iya bada number Motar saboda na zargi motar duk inda mukayi motar na biye damu wataƙil da hukuma zasu shiga za'a iya kama wa anda suka sace Yah Jameel, domin tun fitar mu motar ke bibiyanmu har saida muka kusa gidanmu suka daina binmu”. Cike da mamaki Asma'u tace. “Kai Khausar?”. Kallonta Khausar tayi tare da gyaɗa mata kai kana tace. “Wallahi kuwa Asma'u amma lokacin bamu kawo komai aranmu ba shima kuma Malam Jameel Bai kawo komai ransa ba”. Girgiza kai Ummi tayi kana tace. “Toh ya zamuyi idan an faɗa zai zama matsala zasu kashesa tunda sunce basu yarda afaɗa wa hukuma ba shiyasa dole muyi hakuri”. Jinjina kai Khausar tayi kana cikin sanyin murya tace. “Toh shikenan Ummi Insha Allah zamu cigaba da yiwa Yah Jameel Addu'o'i Allah ya bayyana shi”. Jingina kai Ummu tayi tare da cewa. “Yawwa shine abinda ya dace Allah yabamu Sa'a”. Wunin wannan ranan haka Khausar tayi ta rarrashin Asma'u da Ummi kana tana sake basu ƙwarin gwiwa kan cewa da izinin Ubangiji M Jameel zai dawo bayan Sallar sala'sar ta koma gida tana isa gida daga bakin. Barandarsu ta jiyo sautin kukan Ramadan cikin sauri ta cire takalminta tare da shiga falon bakinta ɗauke da Sallama. Cike da damuwa ta sauƙe Idanunta akan Ramadan daya kifa kansa kan cinyar Mommy cikin rauni da raɗaɗin ciwo yake jujjuya kansa akan cinyar Mommy kana yana cewa. “Mommy Kaina ciwo!,Mommy Kaina zai fashe!”. Ajiyar zuciya Mommy ta sauƙe Cike da damuwa tace. “Subhanallah Ramadan yau tun safe kake ta cemin kanka na ciwo to meke faruwa ne na baka magani kasha abanza ko dai in kira Abbanka ne akai ka asibiti?”. Cikin tsanananin ciwo ya Girgiza mata kai yayi kana cikin Muryan kuka yace. “Mommy ni dai Banason allura aƙara min magani kar kaina ya fashe”. Khausar kuwa cikin sauri ta cire hijabinta kana ta ƙara sa kusa dashi tare da ɗaura tafin hannunta akan goshinsa lokaci ɗaya zafi ya ratsa tafin hannunta har ƙananan jijiyoyin kansa sun tashi suna harbawa cikin sauri ta kalli idanunsa gani tayi sun kaɗa suyi jawur dasu kana yanayin su ya koma kamar ajuye. Saurin kallon Mommy dake jera masa sannu tayi kana tace. “Subhanallah gaskiya Mommy akaishi Asibiti”. Cikin sanyin murya Mommy ta kalli Ramadan dake ta juyi kana ta kalli Khausar dake cikin damuwa ta fesar da numfashi tare da cewa. “Nima nace aikai shi asibiti amma yace baya Son allura da zaran nace akaisa saiya sa kuka”. Girgiza kai Khausar tayi kana ta sake shafa goshinsa da yayi masifar zafi cike da damuwa tace. “Mommy yaushe za'a biye masa jifa yanda kansa yayi zafi kamar wuta”. Kai Mommy ta gyaɗa kana tace. “Bari akwai maganin da Abbanku yace zai sayo masa yanzu bari idan ya kawo za'a bashi idan Allah yasa ya samu sauƙi shikenan idan kuma abin be lafa ba dole sai mutafi asibitin”. Jinjina kai Khausar tayi tare da cewa. “Toh shikenan Allah ya bashi lafiya Allah kuma ya dawo da Abba lafiya”. Mommy na shafa kan Ramadan tace. “Ameen”. Acan ɓangaren Abban Jameel kuwa ahankali ya miƙe tare da kallon wayarsa kana ya sauƙe Ajiyar zuciya tare da nufar toilet domin ya watsa ruwa baki daya baya jin daɗin jikinsa bakinsa ɗauke da addu'a ya shiga toilet din kana ya fara wanka. Hajiya Karima dake zaune afalon kasancewar itace da girki tayi saurin kallon wayar Abba dake ruri miƙewa tayi tare da isa kan 3sitter ganin number babu suna yasa tayi saurin picking tare da kaiwa kunnenta tace. “Assalamu Alaikum”. Ba tare da mutumin ya amsa Sallamar taba yace. “Ina Mahaifin Jameelu?”. Da sauri ta gyara zaman wayar akunnenta tare da cewa. “Me kuke so ku faɗa min nice mahaifiyarsa”. Cike da gadara Mutumin yayi gyaran murya kana yace. “Dashi muke son magana, muna son muji shin kuɗin mu sun haɗu ne?. Zamu faɗa masa inda za'a ajiye kuɗin sannan kuma da inda za'a zo akarɓi Jameel”. Hajiya Karima kuwa cikin ƙasa da murya tace. “Haba bayin Allah kuji tsoron Allah mana. Yanzu fisabilillah ina zamu samu Million ɗari da hamsin wannan aiba rayuwa bane duk da cewa Mahaifinsa mai kuɗi ne ina zai samu wannan uban kuɗin acikin ƙaramin lokaci kawai dai ku temaka ku rage idan ku akayi wa haka ya zakuji? Gwara dai ana rage mugunta”. Dai-dai lokacin da Abba ya fito daga wankan batare daya gama ba jin alamar muryan Hajiya Karima na magana ƙasa². Yana fitowa ya Fisge wayar ahannunta tare da mannawa akunnensa dai-dai lokacin da mutumin ke magana cikin tsanananin fushi da gadara yace. “Ok haka ma kuka ce. Wato wasa da mu ku keyi kun maida mu bamusan abinda muke ba, toh Insha Allah daga yau har gaban Abadan baza mu sake kiran kuba. Alhj Bashir ya maka kyau duk irin halarcin da gargaɗin da muka maka baka jiba har kuna sake neman ragi”. Cikin tsanananin kaɗuwa, ruɗu, da tashin hankali. Abba ya girgiza kai kana cikin raunin murya yace. “Dan Allah da m...”. Kafin ya ƙarasa yaji ɗit-ɗit-ɗit alamar sun kashe kiran. Cikin wani irin yanayi ya zauna tare da sake kiran layin yaji akashe Aruɗe ya shiga fito da sauran numbers din su yana kira amma baki ɗaya Switch off. Kansa ya dafe da hannunsa na dama yayin da hannunsa na hagu ke riƙe da wayar. Cikin wani irin fushi ya miƙe tare da kallon Hajiya Karima dake tsaye azabure ya ɗaga hannunsa tare da kife ta da mari kana ya sake watsa mata wani gigitaccen marin da saida taga gilmawar taurari cikin wani irin fushi ya cigaba da yarfa mata maruka gefen hagunta da damanta. Muryarsa na rawa yace. “Karima na saki acikin wannan maganar tunda aka fara. Meyesa zaki ɗauka min waya. Karima kin cuceni. Wallahi Karima duk wani abinda ya faru da Jameelu kece sanadi kece kika ja ke kika cutar min da rayuwar ɗana”. Da sauri ya dafe ƙirjinsa dake wani irin zafi kana ya ɗago ya kalleta da idanunsa da suka sauya launi zuwa tsantsar tashin hankali kana yace. “Karima haka nayi dake kina gani ɗazu akan idonki na dawo daga Taraba naje na karamo kuɗi na sake karɓan bashin banki 50 millons yanzu ruwan kuɗi ahannuna Million Ɗari da arba'in da biyar ne Million biyar ne kaɗai ya rage kuma nasan da izinin Ubangiji ba zasu gagara ba zan nemosu amman shine zaki nema min ragi”. Hajiya Karima kuwa kuncinta ta dafe tare da sun kuyar da kanta ƙasa tana mai cike da taraddadi. Cikin rauni da fusata Abba ya cigaba da cewa. “Saboda bake kika haifi min Jameelu ba shine zaki salwantar da rayuwarsa, yanzu da ɗan da kika haifa a cikin kine zaki masa irin wannan abin? Karima kin cutar da rayuwata cuta mafi muni, muddin wani mummunan abu ya faru da Jameelu na bazan taɓa yafe miki ba”. Cikin zubda hawaye Hajiya Karima tace. “Haba Alhj wallahi ni ba haka nake nufi ba, kafahimceni tunda naga wancan karon ma da aka nemi ragin ai sun rage shiyasa nace barin ne mamaka sauƙi”. Dai-dai lokacin Moddibo ya shigo falon idanunsa suka sauƙa akan Abba da jikinsa ke rawa idanunsa sunyi Jawur tamkar zai tsats-tsafo da hawayen jini yayin da numfashinsa ke seizing. Cikin sauri Moddibo ya ƙara sa tare da riƙe Abba kana ya zaunar dashi akan kujera cikin sanyin murya yace. “Abba mai ya faru?”. Kasa cewa komai Abba yayi baki ɗaya baya cikin hayyacinsa numfashinsa sai kai koma yake cikin rauni da ficewar hayyaci yace. “Karima kin cuceni Meyesa zaki min haka. Meyesa zaki ƙuntata min ta wannan hanyar!?”. Cikin sauri Hajiya Turai ta shigo ganin halin da Abba ke ciki yasa kai tsaye ta wuce Bedroom ɗinsa tare da ɗauko masa magani kana ta kira Dr Muktar ya ɗagawa tace. “Dan Allah Dr maza kazo jikin Alhj ya tashi gaba ɗaya ma numfashinsa sama yake yi”. Da Ok Dr ya Amsa kana ta katse kiran tare da fitowa da magani ta ɓare tare da miƙa masa. Cikin azabebben rawan da jikinsa keyi ya ture hannunta tare da cewa. “Ba zan shaba Karima kin cuceni kin cutar da rayuwata, kin datse min farin cikina. Meyesa haka Karima duk abinda ya samu Jameelu Karima kece sanadi idan wani abu ya samu Jameelu Karima kece sanadi!”. Ganin alamar baya cikin nutsuwarsa yasa Moddibo cewa. “Dan Allah Abba ka kwantar da hankalin ka”. Girgiza kai Abba keyi yana cewa. “Karima kin cuceni kin cutar da rayuwata kin katse min farin cikina”. Zama Moddibo yayi kana cikin sanyin murya ya shiga Furta. _“Innalillahi wa'inna ilahi rajiu'n Hasbunallahu wani'imal wakil Allahumma Ajirni fii musibati wa'ahlifli khairan minha La'ilaha Illah anta subhanaka Inni kuntu Minal Zhalimin la haula Wala ƙuwwata Illah billahil aliyul Azhim”_. Ahankali Abbah yafara bin bakinsa yana karato adduo'in tun yani yi Aransa har yafara afili. Hajiya Turai kuwa number Dr Muktar ta sake Kira yana ɗagawa tace. “Dr kayi sauri dan Allah ina katsaya har yanzu baka zoba kuma na faɗa maka jikin Alhj ya tashi gashi mun basa magani yaƙi sha”. Cikin sauri Dr Muktar yace. “Gani nan na fito dama yanzu zan wuce asibiti amma yanzu na kusa gidanku ma ina ƙara so wa”. Cike da damuwa tace. “Toh shikenan sai kazo dan Allah kayi sauri”. Ta ida maganar tare da katse kiran kana ta juya ta fice. Moddibo kuwa ciki sanyi ya riƙe hannun Abba tare da cewa. “Abba dan Allah kayi haƙuri ka cigaba da Addu'a”. Kai Abba ya gyaɗa kana ya cigaba da maimaita adduo'in but still ɓarin da jikinsa keyi bai dai naba saima ƙaruwa da yake. Dai-dai lokacin da Dr Muktar yayi hong mai gadi ya buɗe masa kana cikin sauri ya fito daga motar hannunsa riƙe da fest aid box Hajiya Turai dake Safa da marwa a coumpund ɗin ta masa jagora zuwa ɗakin suna shiga Dr Muktar ya zauna kan 1sitter kana ya buɗe Aidbox ɗin sa tare da gwada Bp Abba. Cikin sauri ya kalli Abba tare da cewa. “Subhanallah jinin Alhj ya hau sosai na faɗa muku ku daina kawo duk wani abu da kuka san zai ɓata masa rai, ko kuma tayar masa da hankali”. Ya faɗa tare da ciro sirinji kana yace. “Alhj bari nayi maka allura baki ɗaya damuwa yayi masa yawa”. Ajiye sirinji Dr Muktar yayi kana ya balli magunguna ya miƙa masa tare da cewa. “Alhj gashi kasha”. Girgiza kai Abba yayi cike da rauni yace. “A'a bazan shaba”. Asanyaye Dr Muktar yace. “Ayyah Alhj dan Allah kasha mana”. Girgiza kai Abba yayi tare da cewa. “A'a bazan shaba menene amfanin rayuwata matuƙar dai bazan iya temakon Jameelu na ba. Meye riban cigaba da rayuwata matukar Jameelu na baya tare dani?”. Cikin sauri Moddibo ya Girgiza kai tare da cewa. “Subhanallah Abba kada kace haka kada zafin damuwa yasa mu kaucewa lissafin hankali da na Musulunci Abba kayi addu'a dan Allah ka karɓi maganin kasha Abba. shin yakakeso nayi idan har kaima ka faɗi ciwo ya kwantar da kai”. Cikin tausayawa ya kalli Abba idanunsa cike da ruwan hawaye kana yace. “Abba na tabbatar ko da J na nan bazai yi farin ciki da haka ba Abba dan Allah kayi haƙuri kasha maganinka, ganinka cikin dauriya shike bani ƙarfin gwiwa Abba bazan so ganin wani mugun abu yasa Meka ba. Idan har wani abu ya sameka Abba ya zanyi da rayuwata!?”. Ya ida Maganar tare da miƙawa Abba maganin karɓa Abba yayi tare da kaiwa bakinsa ya haɗiye miƙewa Dr Muktar yayi kana yace. “Alhj bari a maka Allura”. Kai Abba ya gyaɗa kana Dr Muktar ya masa bayan ya masa ya juya ya fice. Sannu Ahankali Abba ya fara maida numfashi kana ya jingina bayansa da jikin kujera ahankali numfashinsa ya fara dai-dai-ta Atake zufa ya shiga tsats-tsafo masa agabaki ɗaya ilahirin jikinsa. Moddibo kuwa ganin haka yasa ya miƙe ahankali tare da ɗaukan remote ɗin AC ya kunna kana ya dawo ya zauna agefensa. Matsawa kusa da Abba Hajiya Turai tayi kana ta ɗauki hankief ta shiga goge masa zufa, cikin sanyin murya tace. “Sannu Alhj Ubangiji ya sawwaƙa maka, ka kwantar da hankalin ka insha Allah babu abinda zai samu Jameelu sai al'khairi”. Kallonta yayi amma baice komai ba. Moddibo ma ahankali ya dawo kusa dashi ya zauna kana cikin sanyin murya yace. “Abba ka kwantar da hankalin ka insha Allah babu abinda zai samu J Abba yanzu fa abinda ya kawoni da mukayi waya kace ansamu kudin kwata kwata Abba yanzu fa Million biyar ne ya rage akan kuɗin da muke nema ai abu yazo ƙarshe insha Allah babu abinda zai samu J, Kuma ma kafin inzo nayi waya da Ummi tace akwai wasu gwala-gwalai guda biyu gobe zata kaisu Taraba, da akan yau zata kaisuma to dare yayi, ta kuma cemin in sha Allah zasu iya kai two million. Kajifa alamomin nasara Abba meye zai tayar maka da hankali!?”. Ahankali Abba ya ɗago jajayen Idanunsa tare da kallon Moddibo kana ya kalli Hajiya Turai sai kuma ya maida kallonsa kan Hajiya Karima dake tsaye cikin rauni ya nuna ta da yatsa kana yace. “Karima ce nashiga wanka suka kira. Karima ta ɗauka wai tana musu maganan ragin kuɗin nace ta nema min ragi ne? Tabarni mana Jameelu ba ɗana bane ai zan fashi ɗana amma Meyesa Karima zata min haka!?”. Moddibo kuwa cikin wani azabebben tsinkewar zuciya ya riƙe kansa tare da cewa. “Innalilahi wa'inna ilahi rajiu'n. kika nemi ragin kuɗi kuma Aunty Karima amma gaskiya baki kyauta mana ba”. Cikin tsananin tsoro da fargabar abinda hakan zai haifar yaci gaba da cewa. “Amma gaskiya baki kyauta manaba, ai wannan mugunta ne an saki ne ko kuma annemi wani temako awajenki fisabilillahi? wallahi kin cutar damu wannan shine cuta mafi muni da kika mana bayan kinji gargaɗin da sukayi”. Ya ƙarashe mgnar cikin raunin murya yana jin zuciyarsa na wani irin zafi da karaya. Cikin sauri Hajiya Turai ta kalli Hajiya Karima tare da Girgiza kai cike da takaicin halayyar ta tace. “Idan har ba tayi haka ba ai bata cika Yadukko ba, ai dama baka sanin mai sonka da gaskiya sai kashiga wani hali, wasu kuma burinsu su samu hanyar da zasu musguna wa rayuwarka suke nema”. Kallon Hajiya Turai Hajiya Karima tayi kana ta kalli Abba da Moddibo cikin Muryan kuka tace. “Agaskiya ni anyi min bahaguwar fahimta nima Ina son Jameelu tamkar ɗa yake awajena fa, ke Hajiya Turai da kike wannan maganar nida ke waya fara zama da Jameelu ne?”. Banza Hajiya Turai tayi da ita tana jin wani irin takaicin abinda ta aikata aranta. Sannu Ahankali bacci ya fara fisgar Abba saboda magani da Alluran da aka masa nan take Bacci ya ɗauke sa kwanciya Moddibo ya gyara masa akan kujeran kana ya miƙe tare da ɗaukar key ɗin motarsa zuciyarsa cike da rauni damuwa da tashin hankali duk sun bayyana afuskarsa. Yana fita yashiga motarsa tare da yimasa key yayin da hawaye suka cika kwarmin Idanunsa Driving yake yana sake try numbers din da suke kira kasancewar duk lokacin da suka kira saiya yi copy amma baki ɗaya Swich off. Ahankali ya fito da Number M Jameel kana Yayi dearling cikin ikon Allah yaji wayar tashiga tana ringing lokaci ɗaya ya shiga cikin matsanancin farin ciki afili ya furta. “Yau kuma wayar J tana shiga”. Cikin sauri ya juya akalar motarsa zuwa gidan Ummi kana ya Parking awaje tare da buɗe gate ya shiga coumpund ɗin yana cewa. “Ummi! Ummi!! Ummi!!!”. Ummi dake tsaye Atsakiyar falo tayi saurin fitowa tare da cewa. “Na'am Babana me yafaru?”. Cike da walwala yace. “Ummi wayar J ɗina yana shiga yau”. Cike da farin ciki Ummi ta ware ido kana tace. “Wayar Jameelu yana shiga?”. Kai Moddibo ya gyaɗa still da murmushi afuskarsa ya gyaɗa mata kai kana yace. “Wallahi yana shiga Ummi bari ma kiji”. Ya faɗa tare da dearling number M Jameel aikuwa ya shiga ya fara ɗut-ɗut-dut cikin Sauri ya samata akunne da sauri Asma'u da Bashir dake Bedroom suka fito jiyo sautin su Ummi cikin farin ciki. Murmushi Ummi tayi tare da cewa. “Bari in Kira nima". Ta ida maganar tare da dearling number kasancewar wayar na hannunta still ya shiga yana ringing. Cikin sanyi ta juya ta kalli Moddibo tare da cewa. “Babana to ya baya ɗauka kuma?”. Cikin wani masifaffen tsinkewar zuciya da tsoro Moddibo ya kalleta cikin ƙoƙarin ɓoye tsoronsa yayi Murmushi tare da cewa. “A'a Ummi Insha Allah tunda har wayarsa tana shiga zai ɗaga mu cigaba da kira da izinin Ubangiji zai ɗaga Agaskiya Ummi yau naji sanyi”. Murmushi Ummi haram Asma'u, da Bashir. “Har naji hankali na ya dan kwanta wayar J ɗina ya shiga, kinga farko kafin mu rasa shi kiran wayarsa muka fara rasawa Ummi, yanzu kuma Insha Allah mun samu kiran wayarsa shi zamu ƙara samu next da izinin Ubangiji”. Kai Ummi ta gyaɗa tare da cewa. “Ameen”. Cikin jin sanyi Asma'u tayi murmushi kana tace. “Alhamdulillah wayar Yah Jameel ya shiga gaskiya munyi farin ciki”. Malam Ahmad daya fito daga wanka ya fito coumpund ɗin fuskarsa ɗauke da murmushi kana yace. “Alhamdulillah Asma'u maza kawo musu abinci suci tunda mun samu wayar Jameelu ya shiga maza kawo musu abinci”. Moddibo kuwa kallon Malam Ahmad yayi kana yace. “Nikam ma Malam baki ɗaya cikina ya cushe baki ɗaya farin ciki ya cika min cikana”. Murmushi Ummi tayi kana tace. “Nima cikina ya cika baki ɗaya farin ciki nake ji”. Jinjina kai Malam Ahmad yayi tare da cewa. “Dan Allah ku zauna kuci abinci wayarsa muka fara rasawa yanzu kuma wayarsa muka faru samu insha Allah shi ma zamu sameshi nan kusa ”. Dai-dai lokacin Asma'u tazo ta ajiye musu abincin. Tun ɓatan M Jameel sai yau Ummi da Moddibo sukaci abinci mai nauyi acikinsu duk da ba dayawa suka ciba. Miƙewa Moddibo yayi kana yace. “Ummi bari naje in faɗawa Innayi ta tayamu farin ciki”. Kai Ummi ta gyaɗa tare da faɗin. “Aikam dai gwara kaje”. Ficewa yayi tare da tafiya Driving yake Cike da farin ciki har ya isa gida yana zuwa ya shiga sashen Innayi. Innayi dake ki shimfiɗe ta miƙe kana tace. “Alhamdulillah Moddibo naga kana cikin farin ciki da alama akwai labari mai daɗi?”. Kai ya gyaɗa still Fuskarsa ɗauke da murmushi yace. “Innayi wayar J ɗina ya shiga yau”. Kai Innayi ta gyaɗa tare da cewa. “Alhamdulillah gaskiya munyi farin ciki. Allah ya bayyanar mana dashi”. Ameen ya amsa tare da wucewa sashen sa cike da farin ciki yana shiga ɗaki ya kira layin Malam Arɗo. Malam Arɗo na dagawa yace. “Malam Alhamdulillah yau wayar J ɗina yashiga a cigaba da taya mu da addu'a a masallacai da makarantu”. Cike da farin ciki malam Arɗo yace. “Masha Allah da izinin Ubangiji zai fito Insha Allah zamu cigaba da addu'a”. Awannan daren haka Moddibo Ummi, Asma'u Bashir malam Ahmad da Innayi suka kwana cike da farin cikin shigar wayar M Jameel. Yayin da Aɓangaren Abba ya kwana cikin taraddadi da tashin hankali koda ya farka tsakiyar dare kuka yayi ta yi yayin da Hajiya Karima ke kuka tana basa haƙuri kana tana cewa bada niyya tayi ba. Aɓangaren gidan Lamiɗo ma haka Khausar da Mommy suka kwana azaune da Ramadan da kansa ke masifar ciwo da zaran an bashi maganin da Lamiɗo ya kawo yasha ciwon zai ɗan lafa jimawa kaɗan kuma zai sake tashi tsakiyar dare ya farka ya riƙa kuka dole Ummi ta kira Abba ya kawo masa magani cikin ikon Allah yana sha ciwon kan ya lafa. Washe gari; Moddibo, Malam Arɗo, Ummi Innayi duk wani makusancin M Jameel na cikin farin ciki kana duk wanda ya kira wayarsa zai shiga sai dai ba aɗagawa Wunin wannan ranan haka Moddibo yayi yana kiran layin M Jameel still ba amsa. Zuwa yamma jikin Moddibo ya fara sanyi da lamarin ganin yana kiran wayar M Jameel baya shiga lokaci ɗaya tsoro ya fara kamashi hankalinsa ya tashi Misalin ƙarfe goma na dare yana gidan Abba zaune sun kira Jameel kuma sama da sau ashirin kuma duk kiran yana shiga, sau dai ba'a ɗagawa, su kuma masatan basu kiraba. Yayin da idanun Abba ke kumbure alamar har yanzu jinjinsa bai sauƙa sosai ba. Cikin mutuwar jiki Moddibo ya koma gida kai tsaye sashen Innayi ya nufa bakinsa ɗauke da Sallama ya shiga. Innayi dake zaune riƙe da carbi ta amsa masa cikin raunin Murya yace. “Innayi”. Kallonsa tayi cike da kulawa kana tace. “Na'am”. Ajiyar zuciya Moddibo ya sauƙe tare da fesar da numfashi kana cikin sanyin murya yace. “ Innayi hankalina ya soma tashi wayar J yana shiga ba'a ɗauka sannan mutanen nan basu sake kira ba”. Ajiyar zuciya Innayi ta sauƙe tare da cewa. “Ba komai Moddibo Insha Allah ka kwantar da hankalin ka”. Girgiza kai yayi kana yace. “Anya kuwa Innayi?”. Cikin bashi ƙwarin gwiwa tace. “Ba komai Insha Allah ka cigaba dayi masa addu'a da izinin Ubangiji zai fito yanzu idan sun sake kira kuce musu an samu kuɗin Insha Allah Million biyar bazai gagara ba koda a masallatai anemi temako za'a samu su haɗu”. Kai ya gyaɗa kana yace. “Toh Innayi Allah yasa su kira ɗin dan yanzu kam ma cikon Million ukune”. Cikin jin daɗi Innayi tace. “Alhamdulillah Allah ya bamu sa'a”. Amin yace Sanna ya miƙe ya koma sashen sa cike da damuwa. Washe gari jin sauran kuɗin da ake buƙata, Lamido ya bawa Mommy da kanta ta kaiwa Ummi su sau dai sam basu kuma kiraba. Haka dai rayuwa ta cigaba da tafiya yau kusan kwana ki shida kenan duk lokacin da aka kira wayar M Jameel zai shiga sai dai ba'a ɗauka. Yayinda Ramadan kuwa ke kwana da azabebben ciwon kai idan aka bashi magani yasha ciwo ya lafa anjina kaɗan kuma ya sake dawowa. Ga ɗaya Mommy da kwausar sun shiga damuwa, sun kai asibiti har cikin Taraba anyi hoton kan da duk wani gwaje-gwaje amman babu wani ciwo dake kansa, dan da farima likitocin sunyi zaton brain cancer ne. baki ɗaya yaron ya fita hayyacinsa saboda tsananin ciwon kai. Yau kimanin kwana shida kenan da aka fara samun wayar M Jameel na shiga. Washe garin rana ta bakwai. Da safe bayan an idar da Sallar Asbah Moddibo na fita a masallaci ya kira wayar M Jameel. Cike da mmki tsoro ya janye wayar a kunnenshi sabida jin ance masa Switch off. cikin mutuwar jiki ya nufi gidan Ummi yana shiga ya samu Ummi zaune akan Sallaya hannunta riƙe da Carbi. Cike da ladabi ya gaisheta kana cikin sanyin murya yace. “Ummi”. Kallonsa tayi tare da cewa. “Na'am Babana”. Cikin raunin murya yace. “Ummi na kira wayar J ɗina baya shiga”. Ahankali Ummi ta jingina kanta da jikin kujeran falon kana tace. “Nima na kira wayan Jameelu na baya shiga bansan Meyesa ba Allah yasa al'khairi ne”. Cike da sanyi Middibo yace. “Amin ya Allah in sha Allah ba komai Ummi”. Cikin raunin murya Ummi ta lumshe Idanunta tare da cewa. “Hmmm,Hmmm Ubangiji Allah yabamu ikon cinye jarrabawar da zai jarabce mu”. Cikin sanyi Moddibo yace. “Ameen”. Miƙewa Moddibo yayi kana yace. “Ummi bari naje gidan Abba naji koshi ya kira ya shiga”. Kai Ummi ta gyaɗa Muryanta cike da rauni tace. “Toh”. Cikin sanyin jiki zuciya cike da karaya Moddibo ya nufi gidan Abba yana shiga coumpund ya ga Abba na ƙoƙarin shiga falo dawowansa daga masallaci kenan. Ƙara sawa Moddibo yayi tare da miƙa masa hannu sukayi musabaha kana cikin sanyin murya Moddibo yace. “Abba wayar J ɗina baya shiga”. Ahankali Abba ya sunkuyar da kansa hawaye masu zafi suka shiga bin kuncinsa Shar-shar-shar kamar ƙaramin yaro baki ɗaya ya rame cikin raunin murya yace. “Aliyu dama wayar Jameelu da kira yake shiga. Wani sanyi ne dama hankalina ya tashi tun jiya nake kiran wayar baya shiga, dama ni banyi farin ciki da shigan wayar Jameelu ba. Aliyu inaji Ajikina kamar akwai wani abu da bamu san menene ba jikina na bani ko ina Jameelu na yaje baya cikin walwala na rasa tudun dafawa”. Cikin sauri Moddibo ya runtse Idanunsa zuciyarsa na bugawa da masifaffen ƙarfi kana cikin raunin murya yace. “Abba insha Allah J yana cikin ƙoshin lafiya mu cigaba da masa addu'a amma nima baki ɗaya hankalina yayi masifar tashi”. Cikin rauni da tsanananin tashin hankali suka ci-gaba da tattaunawa. Acan gidan Lamiɗo kuwa Mommy, Khausar da Lamiɗo basu rintsaba a wannan daren. A kan Ramadan suka kwana yanata kuka baiyi bacci ba. Washe gari Bayan an idar da sallan Asbah Hajiya Bunayya ta shigo falon Mommy ahankali Ramadan dake kuka ya miƙa mata hannu kana cikin wata raunan'niyar murya mai cike da wahala yace. “Ummah! Ummah! Kaina zai fashe kaina zai faɗi Wayyo Allah na Kaina! kaina”. Baki daya jijiyoyin kansa sun tashi sunyi ruɗu ruɗu dasu yayinda idanunsa sukayi ja. Cike da tausayawa Khausar ta ɗaura tafin hannunta na dama akan goshinsa Idanunta cike da ruwan hawaye kasa riƙe hawayen ta tayi jin yanda kan ke harbawa da masifar ƙarfi. Kuka sosai Ramadan keyi kana cikin tsananin radaɗin ciwo ya riƙo hannun Mommy kana yace. “Wayyo Mommy Kaina zai fashe. Mommy Kaina Wayyo zan mutu Mommy Zan mutufa”. Wani irin miƙa Ramadan yayi tare da cewa. “Momyyyyy zan mutuuuu”. Cikin sauri Lamiɗo da yanzu ya shigo ya karɓesa ganin yanda idanun yaron suka juya da sauri ya fara ɗan bubbuga kumatunsa yana cewa. “Ramadan! Ramadan!”. Wani irin juyawa Idanun yaron yayi tare da wulƙitawa kana yaja dogon numfashi....! *Zuwa yanzu dai mun gama ratsa tsakiyar labari babi-babi na zaren na dab da fara warware wa.* By *GARKUWAR MARUBUTA* [30/07, 1:40 PM] Halimatu A/rahman Sadeeya: *LITTAFIN SAKAYYAH NA KUDINE KO KIN GANSHI A WASU WURAREN DA BA CIKIN GROUPS NA DANA BUƊE NA SAKAYYAH BAto na satane, 1k ne kacal kuɗin littafin SAKAYYAH yar uwa ki biya ki karanta cikin Aminci da salama babu haƙƙin kowa a kanki 0661110170 GTBank AISHA ALIYU GARKUWA sai ki turo min shaidar biyanki ta WHATSAPP 09097853276, kiyiwa Allah da Manzonsa ku dena fidda min littafina, in dai kin san kin sayane dan ki turawa wasu, dan Allah ki gaya min in mayar miki da kuɗinki🙏🏻🙏🏻Dan Allah nace ba dan niba* Isrnejny. Moddibo kuwa cike da mamaki da tsoro ya maimaita 200 Millions asaman laɓɓansa, he can't believe or imagine zasu iya tambayar wannan maƙudan kuɗin how cames kidnapper zasu tambayi kuɗin fansa kamar sun sace ɗan shugaban ƙasa. Rintse idanunsa yayi tare da cije labɓansa na ƙasa lokaci ɗaya jijiyoyin kansa suka tashi sukayi ruɗu-ruɗu dasu. Dafe kuncin Hajiya Karima tayi da hannunta duka biyu kana ta kyale baki tare da cewa. “Ohh Allah ya kawo mu wani zamani ka haifi ɗa sannan wasu ƙartin banza da wofi su saka kasa ke sayan sa bafa Millions biyu ba, Ba ashirin ba, Ba hamshin ba, Ba ɗari ba, har Millions ɗari biyu sai kace abin Masifa ko dan sunyi zaton Jameel ɗan Aliko ɗan Gwate ne, shi, ka haifi ɗa kasha wahalar ciyar dashi shayar dashi tufatar dashi biya masa makaranta sannan ace ka sake siyan sa”. Dafe kai Abba yayi da duka hannunsa biyu baki ɗaya ilahirin jikinsa rawa yake kar-kar-kar tamkar mazari yayin da idanunsa suka kaɗa sukayi jawur tamkar garwashi. Dai-dai lokacin Hajiya Turai tashigo baki ɗaya tayi zuru-zuru da ita. Idanunta sun kaɗa sunyi jawur dasu ganin halin da Abba ke ciki yasa tace. “A'a Alhj Lafiya Subhanallah”. ta faɗa tare da nufar Bedroom ɗin sa ta da buɗe drawer ta ɗauko naganinsa ganin alamar hawan jinjinsa ne ya tashi tare da manna waya akunnenta bayan kamar second uku tace. “Hello Dr Muktar dan Allah kazo yanzu ina ganin kamar hawan jinin Alhj ne ya tashi”. Cikin raunin murya Abba ya ɗago kai ya kalleta tare da cewa. “A'a ki bari ba sai Dr yazoba, ki bani maganin kawai”. Kai ta gyaɗa kana cikin sauri ta zuba masa ruwa a glass cup ta miƙa masa tare da bara masa maganin karɓa yayi ya afasu abakinsa ya haɗiye. Sannu a hankali ya fara maida numfashi sama-sama yana jin bugun zuciyarsa tare da sarawan da kansa keyi ya fara raguwa amma still hannunsa na dafe da kansa. Ɗago Idanunsa yayi tare da kallon Moddibo daya zuba masa Idanu kana ya kalli gefen damansa Hajiya Turai ce durƙushe Idanunta cike da hawaye lumshe idanunsa yayi kana ya shiga tunani kwata-kwata kuɗin dake cikin account ɗinsa tsuran kuɗi, gaba da baya Million Sha biyu ne wanda yake tunanin da sun cika Ashirin zai bawa M Jameel saboda ya habɓaka Company daya bashi, da ƙarfi ya sake rintse idanunsa tare da dafe kansa tuno wa da yayi acikin Million Sha biyu ma akwai cikon kudin hajji nashi da na matansa da zai cika ta, baki ɗaya tunaninsa ya tushe ina yasan zai fara kai kadaransa asiya masa su cikin gaggawa kuma da daraja sannan abashi kuɗin cikin tsanananin tashin hankali yace. _“Ya Ilahi ya lillahi ya mujibud da'awati ya hayyu ya ƙayyum bi rahma tika astaghisu lahaula wala ƙuwwata illa billahil aliyul azim”_. Abin da yake maimaitawa kenan asaman laɓɓansa. A hankali Moddibo ya matsa kusa dashi cike da tausayawa yace. “Colm down Abba ka nutsu ka kwantar da hankalin ka everything will be fine by the grace of Allah”. Cikin sauri Abba ya riƙo tsintsiyar hannun Moddibo tare da cewa. “Aliyu Why should I find 2 hundred Millions?”. Aliyu mai zan fitar in sayar dashi cikin gaggawa in Samu kuɗi?. Aliyu bani da ko Million ashirin acikin account ɗina,kaji kuɗin da suka kira fa”. Kallonsa kawai Moddibo keyi cike da tausayinsa Cikin raunin murya Abba ya cigaba da cewa. “Aliyu kwanan nan na cire kuɗi na siya filin nan kuma shima gaba ɗaya filin dana siyeshi 25 Million ne da ace suna nan kaga kuɗin akwai ɗan gwaɓi ahannu na”. Sai kuma ya sauƙe numfashi tare da sake damƙe hannun Moddibo acikin nasa kana yace. “Ina da kadaran da zan iya sayarwa amma ta yaya awani lokaci zan samu ace ansiya se anbani kuɗina sannan na wane”. Kasa ƙara sa maganar yayi kawai saiya janye hannunsa dake cikin na Moddibo ya rufe fuskarsa yana mai furta. _“Allahumma Ajirni fii musibati wa'ahlifli khairan minha Hasbunallahu wani'imal wakin La'ilaha Illah anta subhanaka Inni kuntu Minal zhalimin”_. Hajiya Karima dake dafe da kuncinta ta ɗago kai tare da kallon Abba kana tace. “Alhj ai dole dama za ayi ciniki dasu idan yaso sai anemi ragi”. Moddibo kuwa kai ya girgiza tare da kallon ta kana yace. “Idan da ace sunzo mana da sauƙi da kuma Imani acikin zancen zamu iya hakan amma fa kiga yanda idan sunyi magana sai su yanke mana kiran baza su tsaya suji ta bakin muba sai sun kwana ɗaya ko biyu kafin su sake kiran mu”. Da ƙarfi ya runtse Idanunsa tare da cije labɓansa na ƙasa kana ya cigaba da cewa. “Basa tunanin shin wani irin yanayi ko hali zamu kasance aciki ba yaya zamuyi, da wannan kuɗin da suka kira”. Ya ida maganar cikin raunin murya. Ajiyar zuciya Abba ya sauƙe kana yace. “Nima abinda nake tunani kenan idan nace musu babu zasu iya yiwa Jameel Illah”. Girgiza kai Moddibo yayi tare da cewa. “Abba kar ma kace musu babu sai muyi ƙoƙari duk yanda zamuyi mu haɗa kuɗin nan muyi ƙoƙari mu basu”. Ahankali Abba ya furta. “Ya Salam”. Hajiya Turai kuwa cikin matsanancin kuka ta kalli Moddibo kana ta maida kallonta kan Abba tare da cewa. “Ai abayar ɗin yafi Alhj duk wani abinda kake dashi ka sashi akasuwa kawai asamu asayar akarɓo Jameel meye fi maka Jameel aduniyar nan Alhj, kawai asayar da komai akai musu kuɗin akarɓo shi”. Cikin sauri Hajiya Karima ta kalli Hajiya Turai kana tace. “Kamar ya asaida komai Hajiya Turai kifayi tunani akan abinda kike faɗa idan aka sayar da komai muku mu murayu aya kenan?”. Sai kuma ta maida kallonta kan Abba kana ta cigaba da cewa. “Alhj ya za ayi ɗauki irin wannan maƙudan kuɗin amulmula abasu kaga idan wa'annan ƴan Kidnapping din da suka kinnafe Jameelu sunji dadi an basu abinda suke so to wasu kuma ai sauran ƴaƴan zasu zo su kwashe”. Ta ida mgnar tare da sauke numfashi kana ta cigaba da cewa. “Suma sauran ƴaƴan sai aje a kinnafesu su kuma idan kuɗin da za'a fanshe su bai rage ba ya za ayi kenan. A gaskiya wannan ba shawara bace ace za aɗauki wannan maƙudan kuɗin abasu sai kace ba asha wahala wajen ne mansu ba”. Ahankali Moddibo ya ɗago kumburarrun Idanun sa ya kalli Hajiya Turai dake dafe da ƙafaɗan Abba tana sharɓan kuka kana ya maida kallonsa kan Hajiya Karima data zabga tagumi. Girgiza kansa yayi. Sosai hankalin Abba yayi masifar tashi yama rasa wani irin tunani zaiyi Aransa ya gaza tantance abin cewa. Sannu a hankali idanunsa suka fara lumshewa jikinsa ya saki baya yaja tare da gyara kwanciyarsa akan 3sitter tare da lumshe idanunsa Atake Bacci ya ɗauke sa sabida magungunansa da Hajia Turai ta bashi yasha sun jiƙa sunbi jininsa. Ajiyar zuciya Moddibo ya sauƙe tare da miƙewa kana yai musu sai da safe tare da ficewa yashiga motarsa kai tsaye gidan Ummi ya nufa. Awaje yayi Parking motarsa kana ya fita iska na kaɗa ko wani sashe na jikinsa ahankali ya murɗa handle din ƙofar ya tura bakinsa ɗauke da sallama ya shiga. Idanunsa suka sauƙa akan Ummi dake zaune kan Sallaya hannunta riƙe da Carbi yayin da Malam Ahmad ke zaune gefenta yana rarrashin ta. Ganinsa yasa Ummi ta ajiye carbin dake hannunta kana ta maida hankalinta kansa,Anutse Moddibo ya ƙara sa tare da miƙawa malam Ahmad hannu sukayi musabaha kana ya koma ya zana agaban Ummi. Jin Sallamar sa yasa Asma'u da Bashir suka fito daga Bedroom tare da zama gefe da gefen Ummi ya zamana sun sashi a tsakiya kana cikin raunin murya suka gaishesa atare zuwa lokacin shima Bashir kuka yake sosai duk yayi zuru-zuru. Ahankali Ummi ta zubawa Moddibo Idanu kana cikin sanyin murya tace. “Babana ya akayi sun sake kira?”. Kai ya gyaɗa tare da sun kuyar da kansa ƙasa kana yace. “Eh”. Ajiyar zuciya ta sauƙe tare da cewa. “Me suke buƙata?”. Still Kansa na ƙasa yace. “Ummi kuɗi suke so”. Numfashi ta fesar kana tace. “Kuɗi suke so?”. Kai ya gyaɗa amma bai ce komai ba. Cikin tsira masa ido tace. “Kuɗi kamar nawa suke so?”. Cikin rauni ya kalleta kana ya kalli malam Ahmad, Asma'u da Bashir ya fesar da numfashi tare da cewa. “Ummi kuɗin suna da yawa kuɗin da suke buƙata sun wuce zatonmu”. Gyara zama tayi kana tace. “Toh Meye amfanin kuɗin mahaifinsa?, Meye amfanin kuɗin Babansa?,Menene amfanin duk tattalin da yake yi!?”. Girgiza kai Moddibo yayi kana yace. “Ummi kuɗin sun wuce tunanin mai tunani!?”. Ɗa gowa Ummi tayi tare da tsira masa ido kana tace. “Kamar nawa suke buƙata Babana?”. Cikin raunin murya da alamar sarewa Moddibo yace. “Ummi har Million ɗari biyu suke buƙata”. Cikin wani irin yanayi mai cike da rauni, tsoro, mmki Ummi taja ajiyar zuciya kana ta maida kanta ta jingina da jikin kujeran da Malam Ahmad ke zaune tare da lumshe Idanunta kana Muryanta na rawa tace. “Ƙarya sukeyi ba kuɗin suke so ba so suke su kashe min Jameelu lallai Mahaifinsa mai arziƙi ne amma be kai matakin da za'a matsesa lokaci ɗaya ace ya fito da Million ɗari biyuba, kawai dai yaudarace suke mana anya ma Jameelu yana raye kuwa?”. Cikin sauri Moddibo ya girgiza mata kai kana yace. “Yana raye Ummi ina ji ajikina J yana raye kuma na faɗa miki munyi magana dashi”. Girgiza kai tayi tare da cewa. “Yau da suka kira kunyi magana dashi?”. Shiru yayi yana kallonta amma baice komai ba. Kallonsa Ummi tayi cikin muryan kuka tace. “Babana ka faɗa min gaskiya tsakanin ka da Allah yau kunyi magana dashi?”. Girgiza mata kai Moddibo yayi tare da faɗin. “Ummi ba muyi magana dashi ba, amma naji muryan J ƙasa-ƙasa yana cewa Abba abasu duk abinda suke so”. Ajiyar zuciya Ummi ta sauƙe tare da rintse idanunsa kana tace. “Babana ka tabbatar gaskiya kake faɗa min?” Jinjina kai Moddibo yayi kana cikin sanyin murya yace. “Wallahi Wa rabbul Khaba Ummi naji muryan J ƙasa. yana magana bawai sun bashi bane amma naji yana magana”. Kuka Asma'u da Bashir suka fashe da shi atare kana lokaci ɗaya suka haɗa baki wajen cewa. “Innalillahi wa'inna ilahi rajiu'n ya Allah ka kuɓutar da Yah Jameel Ubangiji kada ka basu ikon cutar dashi ya Allah kaine gatanmu Yah Jameel shine ka wakilta da isar mana gatanmu ya Allah ka karesa da karewaka”. Numfashi Malam Ahmad ya fesar kana cike da tausayawa yace. “Asma'u ba kuka ya kamata kuyi ba addu'ar mu Jameelu ke buƙata idan kuna kuka ya kuke so Ummin ku tayi?”. Cikin sheshsheƙan Kuka Asma'u tace. “Abba Yah Jameel fa Yah Jameel yana cikin mawuyacin hali Abba kaji fa maƙudan kuɗin da suke buƙata Abba ya za'ayi mu samu irin wannan kuɗin mu karɓo Yah Jameel Abba Ina tsoron kada su cutar mana dashi”. Girgiza kai Malam Ahmad yayi cikin sanyin murya yace. “Insha Allah da izinin Ubangiji babu abinda zai samu Jameelu, ko wani bawa da kalar tashi ƙaddaran tun kafin a haifi Jameelu Ubangiji ya zana masa ƙaddaransa muyi masa addu'ar Allah ya sauƙaƙa mana zafin ƙaddararsa”. Jinjina kai Moddibo yayi yana jin wani irin azabebben zafi aƙirjinsa. Kallon Moddibo Malam Ahmad yayi kana yace. “Moddibo mai Yakamata ayi acikin wannan al'amarin!?”. Moddibo da kansa ke ƙasa ya ɗago ya kallon Malam Ahmad a hankali yace. “Malam abinda yakamata kawai afara cuku-cukun neman kuɗin nan sai muga abinda zai kasance”. Girgiza kai Ummi tayi still tana jingine da jikin kujera tace. “Babana ina zamu samu kuɗin nan Million ɗari biyu fa da ace Million biyu suka ce koni kaina ma zan bada su”. Ta faɗa tare da ɗaukar wayarta tayi checking balance kana tace. “Gashi yanzu anan ina da Million ɗaya da dubu ɗari huɗu da hamsin da ɗaya sannan kuma ba matsala gobe in Allah ya kaimu zan tafi cikin. Taraba zan kai gwala-gwalaina”. Sai kuma ta ɗan tsaya, jin numfashin ta na yankewa, da ƙarfi ta fizgo numfashin tare da cije labɓanta na ƙasa hawaye cike da Idanunta murya na cike da rauni ta cigaba da cewa. “Zan saida su inga nawa zan samu ajikinsu zan haɗa harda na Asma'u sannan, motata itama zan saidawa muga nawa zan samu awurina”. Jingina kai Malam Ahmad yayi kana cikin sanyin Murya yace. “Har gidan nan ma asashi a. Kasuwa asayar dashi”. Kallonsa Moddibo yayi tare da girgiza kai kana yace. “A Malam ayi haka”. Kai Malam Ahmad ya gyaɗa kana yace. “Asiyar Moddibo menene Jameelu baiyi mana ba aduniyar na, kasancewar sa atare damu shiyafi mana komai”. Ahankali Ummi ta ɗago kanta tare da tsira masa ido hawaye na bin kuncinta ta sani fili dai filinsa ne halalinsa mallakinsa, amma baki ɗaya ginin dake ciki Jameel ne ya musu bayan yasa an buge tsohon ginin taɓon. Girgiza kai tayi cikin rauni tace. “A'a ba sai anyi haka ba bari muga abinda Mahaifinsa zai samu”. Girgiza kai Malam Ahmad yayi tare da kallon Asma'u da Bashir da har zuwa lokacin suke kuka a hankali ya fesar da numfashi tare da cewa. “Ni dai na sadaukar da wannan gida ga. Jameelu wallahi na yafe masa shi duniya da lahira na amince asa shi akasuwa muddin za a samu masu siya, to asa shi akasuwa mu samu muga aƙalla dai awajen mu ace an samu Million goma kuɗin zaifi gwaɓi”. Sun kuyar da kai ƙasa Ummi tayi hawaye masu masifar zafi suka zubo mata. Hannunta Moddibo ya riƙe cikin sanyin murya yace. “Ummi dan Allah ki daina wannan kukan idan kina kuka muku ma ya zamuyi Ummi babu abinda J ke buƙata awajen mu face addu'a ganin ki awannan yanayin naya sake raunatamana zuciya”. Kai Malam Ahmad ya gyaɗa kana yace. “Sosai ma wannan kukan da kike Fatima saidai ya haddasa miki wani ciwon amma babu amfanin da zaiyi dan Allah ki daina ki cigaba da yi masa addu'a. shi kansa ba zaiso ace kina masa kuka ba”. Kai ta gyaɗa tare da share hawayen ta kamar yarinya kana tace. “Na daina Insha Allah zan cigaba da yimasa addu'a Ako da yaushe”. Saida Moddibo ya tabbata ta daina kukan kafin ya mata sallama ya fice cike da tausayinsu Driving yake ahankali har ya isa gida yayi Parking kana ya fito ya rufe gate din tare da wucewa sashen Innayi bakinsa ɗauke da sallama. Kwance ya samu Innayi cikin Yanayin damuwa gefenta da Radio tana sauraro wanda ɓatan M Jameel ake sanarwa. Miƙewa tayi ta zauna tare da amsa Sallamar sa kana tace. “Moddibo ya labarin Jameelu?”. Cikin sanyin murya yace. “Innayi sun sake kira ɗazu”. Ajiyar zuciya ta sauƙe tare da cewa. “Toh kunyi magana dashi yana cikin ƙoshin lafiya?”. Girgiza mata kai yayi kana yace. “A'a Innayi bamuyi waya dashi ba amma bisa duk kan Alamu J baya jin daɗin zaman wajen can”. Ahankali Innayi ta jingina bayanta da jikin bango kana ta matsar da Radio gefe tare da cewa. “Dama Moddibo ya za ayi yaji daɗin zaman wannan wajen. kasan yanayin da yake ciki ai dole bazai ji daɗin zaman wannan wajen ba amma me suke buƙata?”. “Innayi kuɗi suka nema”. “Kuɗi suka nema to aisai abasu aje a karɓe shi”. “Innayi kuɗin da suka nema na fitar hayyacine!”. “Kuɗi har nawa suka nema? Da zai zama na fitar hankali”. Dafe goshinsa yayi kana yace. “Innayi Million ɗari biyu suka nema kuma cikin ƙanƙanin lokacin fa”. Ita kam Innayi baki ɗaya lissafin ta sincewa yayi jin maƙudan kuɗin tama rasa nawane, kallon Moddibo tayi tare da cewa. “Dubu ɗari biyu?”. Kai Moddibo ya Girgiza tare da cewa. “A'a ba dubu ɗari biyu bafa Million fa Million ɗari biyu”. Daga kanta sama tayi alamar tunani sai kuma ta kallesa tare da cewa. “Million biyu?”. Still girgiza mata kai Moddibo yayi kana yace. “A'a Million ɗin goma, ashirin, hamsin, ɗari, ɗari da hamshin har ɗari biyu”. Dafe kirji tayi kana tace. “Million ɗari biyu?”. Jinjina mata kai Moddibo yayi. Girgiza kai tayi tare da cewa. “Ban gane lissafin ba Aliyu”. Lips ɗinsa duka biyu ya cije a lokaci guda kana yace. “Ba zaki gane lissafin ba Innayi kuɗi ne masu tarin yawa suke nema”. Cikin sanyin murya Innayi ta jujjuya kanta kana tace. _“Innalillahi wa'inna ilahi rajiu'n Hasbunallahu wani'imal wakin Layukalliful nafsi illa wusɗaha_ Toh yanzu mai Baban nasa yace?”. “Innayi Abbansa bashi da wannan kuɗin a ƙasa kwanan nan dama ya gama yi mana ƙorafi bashi da kuɗi”. Lumshe idanu Innayi tayi kana tace. “Ya Salam ya Ubangiji Allah ka dube mu da idon rahama, ya Allah ka yayemana ya Allah ka sauƙaƙa mana ya Allah ka tsare Jameel ka kare mana shi, Allah ka tseratar da wannan bawan naka”. Cikin sanyin murya Moddibo yace. “Ameen”. Kallon second biyar zuwa bakwai Innayi ta yiwa Moddibo kana tace. “To amma kai Moddibo mai kake ganin zakayi akai?”. Still hannunsa na dafe akansa yace. “Innayi akwai kuɗi awajena zan tattara su in haɗa su muga nawa za'a samu awajena”. Kai ta gyaɗa kana tace. “Yafi kam”. Bayan sun sake tattauna ne Moddibo ya miƙe tare da yi mata Sallama kana ya nufi Sashen sa ahankali ya tura Murfin Kofar shiga tare da mayarwa ya rufe. Kana ya jingina bayansa da jikin da kofar tare da rintse idanunsa sautin murya M Jameel ya farayi masa kai-komo AJ bansan idan nakeba, Lumshe danunsa yayu zuciyarsa na bugawa da masifar ƙarfi yana bada sautin dif-dif-dif cikin sauri ya buɗe Idanunsa jin muryan M Jameel na yawo a kansa yana cewa A.J A.J Kallon kan 3sitrer kurui ji yake kamar zaiga J dinsa a wurin, cikin raunin murya yace. “J Why are you?, Zuciyata zata fashe ya Allah kaji ƙaina ya rabbil Izzati ka dawo da J garemu cikin aminci da salama ya Allah kada ka bawa waɗɗanan azzaluman daman cutar dashi”. Ya kai 15 minutes yana mai jero Addu'o'in cike da rauni, kafin ya miƙe kamar wanda aka mitsina ya nufi Bedroom ɗin sa kai tsaye toilet ya shiga ya watsa ruwa kana ya ɗaura alwala ya fito ya kwanta bisa gadonsa yayi rigingine duk da yasan cewa da wuya bacci ya ɗauke sa amman ya lumshe idonsa domin yau kwana uku rabon da ya samu wani wadataccen bacci sai wani irin azabebben ciwon kai da yakeji tamkar kansa zai rabe da ga wani irin sarawa da yakeyi yana bada wani irin sauti mara daɗi gau-gau-gau!. A hankali ya bude idon sai kuma yayi saurin Lumshe Idanun sabida sarawa da kan yayi masa. Cikin zazzaƙan muryansa mai cike da rauni ya fara raira ƙira'ar Suratul Yusuf hawaye masu ɗumi suka riƙa fita daga idanunsa suna shiga kunnensa cikin wannan yanayin da cikar Sa'adatu da karatun Alqur'ani mai girma ya samar masa, wani irin kiɗimemmen baccin da bai shirya masa ba ya sace sa. Acan cikin baccin sa kuwa zaune ya hangosa akan wata. Tattausan shimfiɗa cikin wani masha'hurin falo mai masifar kyau da ƙawa. Sai dai kima yana ta dariya hartada karketawa, yayinda idanunsa kuma sunyi jawur jikinsa na rawa jin. A hankali ya fara jujjuya kansa yana mai ci gaba da dariyar ya juyo kansa gabansa, jin alamar tafiya tare da wani ƙamshi daya ratsa hancinsa yasa ya ɗaga manyan idanunsa da sukayi luhu-luhu ya sauƙe ganinsa akan Khausar dake zuwa garesa cikin wata iriyar ƙasaitacciyar shiga, ido ya zira mata ko ƙebtawa bayayi har ta isa garesa, a hankali ta zauna gefensa. Tare da tsira masa manyan Idanunta masu haske wanda ke ciki da ruwan hawaye kana ta miƙa masa wani hankief fari ƙall mai masifar ƙamshin turare. Ƙin karba yayi saima lumshe idanunsa da yayi wanda sai lokacin ya samu wasu irin tafasassun hawaye suka samu damar kwaranyowa, hakan yasake kawar da kansa gefe tare da sakin sheshsheƙa. Ahankali Khausar ta matsa gabansa har suna shaƙan nunfashin juna kana ta sanya hankief ɗin ta shiga share masa hawayen cikin wata Sanyayyar murya mai cike da nutsuwa da kuma rauni tace. “Yah Jameel Addu'ar mu yake buƙata ba kuka ba idan kai kana kuka. Toh Ni kuma ya zanyi addu'a za muyi masa kaji ko Abu J”. Ta ida mgnar da kiransa da sunan da ta raɗa masa, tare da faɗawa jikinsa ta fashe da sassayan kuka dai-dai lokacin kuma ya farka. Kansa ya dafe tare da miƙewa ya shiga toilet ya ɗaura al,wala kana ya dawo ya shimfiɗa Sallaya ya fara nafillah yana cigaba da yiwa M Jameel addu'a. Ba tare da yabi ta kan mafarkinba, domin yanzu kam idan da sabo ai yaci ace ya saba da yawan ziyarar kutse da nacin da Khaisar keyi masa cikin rayuwar baccinsa. Washe gari Ummi ta tattara baki ɗaya Sarkoƙi, ta da ɗan kunnen zobe da awarwon Gwal nata dana Asma'u ta shirya ta tafi Tarata. Tana isa kai tsaye babbar kasuwar su ta wuce kana tashiga shagon saida gwala-gwalai ta bayar aka gwada cikin sa'a ta samu sunyi farashi sosai kasancewar Manyan Sarƙoƙine nata dana Asma'u wasu nata tun tana gidan Abban Jameel ne, suka haɗa mata kuɗin ta Naira Million biyu da dubu ɗari huɗu da hamsin sukayi mata transfer dinsu. Daga nan gidan kai tsaye gidan Ƙawarta Hajiya Salma Wanda mijinta ke saida Motoci yawanci awajensa M Jameel ke siyan mota ko kuma can zawa. Mai A dai-dai-tan na sauƙeta ta miƙa masa kudinsa kana ta shiga cikin tangamenen coumpund ɗin daya tsaru kai tsaye ciki ta nufa tare da Knowking ɗin ƙofar kana ta murɗa handle ɗin tashiga bakinta ɗauke da sallama. Hajiya Salma dake zaune akan kujera ta miƙe cikin sauri kana tace. “Hajiya Fatima sannu da zuwa ga wajen zama”. Kai Mommy ta gyaɗa tare da cewa. “Yawwa Nagode”. Sannan ta zauna tare da sakin Ajiyar zuciya. Bayan sun gaisane. Cikin sanyin murya Hajiya Salma tace. “Ayyah Hajiya ashe ga abinda ya faru da ɗana Jameel kuwa?”. Cikin yanayin sanyin ɗaya zamewa Ummu jiki, ta gyaɗa mata kai tare da cewa. “Ummm bari ke dai Hajia Salma duniya tayi min zafi”. Cikin tausayawa Hajia Salma tace. “Ba komai in sha Allah, kada ki damu Hajia Fatima. Ubangiji Allah ya bayyanar da Jameel aduk inda yake Ubangiji ya karesa daga sharrin mai sharri”. Cikin sanyin Murya Ummi tace. “Ameen ya Allah ameen ya hayyu ya ƙayyum”. Cike da tausayawa Hajiya Salma tace. “Wallahi Koda wasa banji ba sai ɗazu da safe Alhj na duba jarida ya gani shine yake sanar min”. Kai Ummi ta gyaɗa kana tace. “Allah sarki ai yanzu anshiga kwana na huɗu kenan. Uhmmm dama nazo kiyiwa Alhj Abdallah magana ne akan ya duba motata ya siya”. Ajiyar zuciya Hajiya Salma ta sauƙe kana tace. “Ubangiji Allah ya tsare Malam Jameel aduk inda yake”. ta faɗa tare da shigewa ciki tsaye ta samu mijin nata yana ƙoƙarin fita Kallonsa tayi kana tace. “Alhj Hajiya Fatima ce ta zo mahaifiyar Malam Jameel”. Kai ya gyaɗa tare da cewa. “Ikon Allah muna shirin zuwa kuma sai gata”. Ya faɗa tare fitowa a tare, a inda Hajiya Salma ta barta anan suka sameta tayi ta gumi. Ahankali Ummi ta ɗago jai tare da cewa. “Alhj Abdallah ina kwana ya gida”. Zama yayi kana yace. “Lafiya lau Hajiya ashe kuma ga abinda ya faru da Malam Jameel”. Kai Ummi ta gyaɗa kana cikin sanyin murya tace. “Eh”. Ajiyar zuciya Alh Abdallah ya sauƙe kana yace. “Wallahi bamu da labari sai ɗazu ina karanta Jarida na gani nake faɗawa Salma tace itama bata da labari dake akwai wani fitar gaggawa daya kamani nace idan nadawo zan kaita da yamma ta gaishe ki”. Ajiyar zuciya Ummi ta sauƙe tare da gyada kai kana tace. “Allah sarki dama Motata ce nazo ka tura adauƙa maka ka ga lafiyarta zan saidata in zaka siya”. Ɗagowa yayi tare da kallonta kana yace. “Motar da Malam Jameel ya siya miki nan?”. Kai ta gyaɗa masa tare da cewa. “Eh shi”. Zaman hular kansa ya dan gyara kana yace. “Amma ai motar bata daɗe ba Hajiya Fatima”. Kai ta gyaɗa Muryanta na rawa tace. “Eh bata daɗe ba Uzurin gaggawa ne ya kama Ni shiyasa zan siyar”. Jinjina kai yayi tare da cewa. “Aikam dama mota ce mai kyau sannan bai daɗe da sayanta ba za tura yaro yaje ya ɗaukota kuma yanzu mugama magana tunda abu na gaggawa ne”. Cikin sanyin murya tace. “Tun baka gani ba”. Girgiza kai yayi tare da faɗin. “Baki da matsala Indai wannan ne zan baki Million shida”. Cikin sauri Ummi tace. “Alhj har Million Shida kuma dama motar yana da tsada kenan?”. Kai ya gyaɗa mata tare da zaro wayarsa acikin aljihu kana yace. “Eh dama Million biyar ne haka ya siyeta toh nasiyeta biyar ɗin kamar yanda ya siya sannan Million ɗayan kuma na bada nawa gudunmawar Ubangiji Allah ya bayyana Malam Jameel”. Ajiyar zuciya Ummi ta sauƙe tare da cewa. “Ameen ya rabbil izzati, ngd Matuƙa". Da sauri ta kalleshi jin yana cewa. “Ki bani account number ki zan miki transfer”. Kai Ummi ta gyaɗa tare da kiramasa number's ɗin. Atake ya mata transfer. Miƙewa tayi tare da yi masa godiya sosai kana ta fito, har ƙofa Hajiya Salma ta rakata kana ta Wuce. Kai tsaye tashar motar Gembila ta nufa, tana zuwa kuwa tayi sa'a mutun ɗaya ya rage, haka yasa ta shiga motar ta tashi. Alhamdulillah sun isa Gembila lfy. A hankali Ummi ke tafiya tana jin wani irin sanyi a ranta tare da Comfedance ga Million ɗaya da dubu ɗari huɗu da dake account ɗinta ga kuma Million biyu da dubu ɗari huɗu da hamsin na Sarkoƙi kana ga Million Shida na mota ya zama tana da tsuran kuɗi ahannunta har Naira Million tara da dubu ɗari takwas kenan. A hankali ta sauƙe wani zazzafafar ajiyar zuciya kana ta nufi gida. Acan ɓangaren Moddibo kuwa ya haɗa duk wasu kuɗaɗe dake hannunsa ya samu Million huɗu da dubu ɗari biyu da hamshin kai tsaye gidan Ummi ya nufa yana Parking ɗin motarsa mai A dai-dai-tan sahu na ajiyeta atare suka shiga falonta. Suna shiga Bayan sun gaisa Ummi tashiga Alart massage tare da miƙawa Moddibo wayarta tare da cewa. “Babana ka kalli kuɗi sunyi gwaɓi”. Amsar wayar yayi tare da Kallon Alart massage ɗin kuɗin kana ya sauƙe ajiyar zuciya tare da cewa. “Masha Allah kuɗi sunyi gwaɓi bari na haɗa dana wajena”. Kallonsa Ummi tayi haka nan taji hawaye na ciko mata kwarmin Idanunta. Cikin sanyin murya Moddibo yace. “Ummi na wurina na bashi da yawa Million huɗu da dubu ɗari biyu da hamsin ne”. Cike da tausayinsa tace. “Toh Allah ya biya. Babana Allah yabamu yanda zamuyi Ubangiji ya saka maka amma ka rage wani abu aciki ka samu na kashewa”. Girgiza kai yayi cikin raunin murya yace. “Ummi wani abu zan rage idan ina da abinda yafi wannan zan ɗauka in bayar akarɓo J naje. nayi magana da dillalai gidan mu na sashi akasuwa in dai za'a samu siyansa akan lokaci. Cikin sauri Ummi ta kallesa tare da cewa. “Gidan ku kuma Babana!?”. Kai ya gyaɗa mata tare da cewa. “Ummi Meye amfanin gidan mai zamuyi da gidan babu wani farin ciki acikisa. Muddin J baya nan fa wanne farin ciki zamuyi. kuma komai da muka rasa zamu iya samu idan J ya dawo gare mu”. Jinjina kai Ummi tayi, Account number dake wayarsa ya fito dashi ya mata transfer kuɗin tare da miƙa mata wayar karɓa tayi ta duba Ajiyar zuciya ta sauƙe tare da kallon kuɗin Naira Million goma sha huɗu kenan cib. Numfashi ta fesar tare da kallon Moddibo kana tace. “Alhamdulillah Babana kuɗi sun cika Million goma sha huɗu bari muje gidan Abban sa tare”. A hankali yace. “Amma Ummi ki bari sai gobe muje wataƙil yau ba zasu kira ba sai goben, amma ni yanzu idan nafi ta zanje wajen Abba muji nawa aka samu awajensa”. Kai ta gyaɗa cikin sanyi tace. “Toh shikenan Babana Allah yasa muji al'khairi”. Kai ya gyaɗa tare da miƙewa kana yace. “Amin. Toh shikenan bari naje yanzu”. Ya faɗa tare da ficewa. Kai tsaye gidan Abba ya nufa bayan yayi Parking ya fito tare da shiga Falon bakinsa ɗauke da Sallama. Abba dake zaune kan 2 sitter ya jingina bayansa da jikin kujera ya amsa masa Sallamar cike da tausayinsa ya zuba masa yana ganin yadda yake tafiya duk ya faɗa acikin kwanaki huɗu ya rame yayi shafal. Ƙara sawa Moddibo yayi tare da zama gefensa kana yace. “Abba ina yini ya kuma haƙurin rayuwa?”. Ajiyar zuciya Abba ya sauƙe tare da cewa. “Alhamdulillah Aliyu ya wajen su Innayi?”. Kansa a ƙasa yace. “Lafiya lau Abba basu sake kira ba ko?”. Girgiza kai Abba yayi tare da fesar da numfashi kana ya runtse Idanunsa cikin sanyin murya yace. “Basu sake kira ba Aliyu”. Jinjina kai Moddibo yayi tare da cewa. “Toh yanzu Abba kuɗi kimanin nawa aka samu awajenka?”. Abba kuwa ahankali ya zame daga kan kushin ɗin ya zauna akan capet tare da fuskantar Moddibo kana yace. “Aliyu na tattara duk abinda yake wajena kana duk wanda nake binsu bashi na tattarasu sannan na nemi temakon bashi duk wanda zan nemi temakonsu sunban bashi baki ɗaya kuɗin dana samu awajena Million hamsin da shida ne, iya adadin kudin dake hannu na kenan, duk ta inda zan buga na buga Aminaina ƴan uwana duk na nemi temako awajen su wasu sun bani kyauta wasu kuma aro na buga shine Million hamsin da shida”. Jinjina kai Moddibo yayi tare da cewa. “Toh Abba kuɗi dai sun ɗanyi gwaɓi gashi awurin Ummi an samu Million Sha uku yanzu kenan muna da Million Saba'in dai-dai a ƙasa. Ajiyar zuciya Abba ya sauƙe tare da fesar da numfashi kana yace. “Alhamdulilah kuɗi sun fara taruwa Amma ɗari biyu fa suka ce gashi ko ɗari cikekke bamu samu ba”. Cikin raunin murya Moddibo yace. “Abba bari mugani idan sun sake kira sai mu rokesu su rage mana idan sun tallafa sun tausaya mana ko bashin banki ne zamu ci sai mu ƙara akai kuɗin ya cikata”. Kallon sa Abba yayi tare da jinjina kai kana yace. “Toh shikenan ba laifi Allah yasa mu dace”. Ameen Moddibo ya amsa kana suka cigaba da hira har Misalin ƙarfe goma. Abba najin ringing din wayarsa Yayi saurin zabura tare da picking kana yayi Sallama. Daga ɗaya ɓangaren cikin bauɗaɗɗiyar murya mutumin yace. “Alhj Bashiru ka haɗa kuɗin?”. Cikin raunin Murya Abba ya gyaɗa kansa kana yace. “Kuyi haƙuri bawan Allah dan Allah kuyi haƙuri wallahi kuɗin nan da kuka faɗa babu su awajena kwata kwata babu”. Daga ɗaya ɓangaren mutumin ya juya tare da kallon M Jameel dake zaune a ƙasa kana cikin wata dakakkiyar murya mutumin yace. “Da alama dai mahaifinka baya sonka”. Jin muryan mutumin agefe yasa Abba saurin cewa. “Don Allah ku bani inji muryarsa”. Cikin wannan bauɗaɗɗiyar murya Mutumin ya wurga wa M Jameel wayar kana yace. “Gashi kaji muryan sa”. Cikin sauri M Jameel ya cafke wayar tare da kaiwa Kunnensa kana cikin sanyin mai cike da rauni mai tada hankalin ɗan Adam cikin murya mai cike da galabaita yace. “Abbana”. Cikin sauri Moddibo ya karɓi wayar a hannun Abba kana yasa a handsfree tare da danna record. Cikin raunin Murya M Jameel yace. “Abba kabasu kuɗin Abba dan Allah ka basu abinda suke so ka fitar dani awannan wajen mana Abbana”. Runtse Idanu Abba yayi kana yace. “Babana zan fitar da kai ina nan ina har haɗawa kuɗin insha Allah zan fitar da kai amma Jameelu duka-duka kuɗin da muka haɗa anan Million Saba'in ne su kuma sunce Million ɗari biyu suke so”. Cikin wata raunan'niyar murya mai cike da masifaffiyar galabaita da neman jin ƙai M Jameel yace. “Abba a saida motocina duka sannan aduba ɗakina akwai kuɗi amma bai cika Million biyu bama dan Allah ahaɗa Abba abasu azo a karɓe ni”. Cikin rauni ya runtse Idanunsa da hawaye suka cika kana yace. “Abba bana son zaman nan babu daɗi ba Ummina ba A.J sannan kaima ba kai wuri ba daɗi dan Allah Abba ka basu duk abinda suke so kazo ka karɓe ni ku saida komai nawa a haɗo kuɗin”. Kai Abba ya gyaɗa tare da ƙoƙarin hana hawayen sa zubowa kana yace. “Babana Insha Allah zan zo in karɓe ka koda raina suke so zan basu amadadin ranka”. Modibbo kuwa tuni wasu irin hawaye masu masifar zafi ke kwaranyo mishi tamkar mace. Fisge wayar sukayi daga hannun M Jameel kana cikin wannan bauɗaɗɗiyar murya Mutumin yace. “Toh kaji dai abinda ɗan ka ya faɗa zamu baka dama ta karshe”. Cikin sauri Moddibo da idanunsa ke rintse ya buɗe tare da cewa. “Dan Allah! Dan Allah!! Dan girman Allah!!! dan darajar Annabi Muhammad (S.A.W) badan muba kamar yanda kuka ce J nada mutunci da kamala toh dan Allah saboda wannan kamalar tasa ku rage mana kuɗin zamu yi muku duk kan biyayya amma ku faɗa mana abinda zamu iya kawo wa”. Daga ɗaya ɓangaren shiru mutumin yayi ba tare da yace komai ba kana bai katse kiran ba. Cikin raunin murya Moddibo yace. “Dan Allah kuyi haƙuri ku rage mana Insha Allah ba zamuyi gardama ba, amma kuɗin hannun mu munyi munyi sun kasa kai adadin da kuke buƙata mu samu su kai adadin da kuke buƙata wannan shine matsalar mu ku temaka ku ragar mana”. Ajiyar zuciya mutumin ya sauƙe tare da cewa. “Wannan Moddibo ne ke magana ko?”. Kai Moddibo ya gyaɗa kana cikin sanyin murya yace. “Eh” Cike da gadara Mutumin yace. “Toh shikenan ku bada Million ɗari da hamsin”. Cikin raunin murya Moddibo yace. “Mungode amma dan Allah ba zaku ƙara rage mana ba?”. Cikin wata razananniyar tsawa Mutumin yace. “Dan ubanka dan ka samu na zabge Million hamshin. Atake to wallahi acikin Million ɗari da hamsin Naira biyar ba zamu rage ba kuma wallahi idan ku ka yarda kuka sake yi mana batun ragi kuɗi to wallahi akan ran Jameel domin kuɗi ne dai mu ki ya rayu ko ya mutu zamu samesu”. Cikin tsanananin tsoro da kaɗuwa Moddibo ya dafe ƙirjinsa yayin da kansa ya sara da masifan ƙarfi. Cikin tsawa Mutumin ya cigaba da cewa. “Yanzu Moddibo gashi kayi magana dashi na ƙarshe wanda ko bacci yake yana kiran sunan ka gashi kayi magana dashi dan wataƙil shine maganarka na ƙarshe kenan dashi matukar dai baku haɗa kuɗin nan ba ku kasake yi mana batun ragin kuɗin to kayi magana dashi na ƙarshe kenan”. ya faɗa tare da wurgawa M Jameel wayar. Cikin sauri M Jameel ya cafke wayar tare da maƙalawa akunnensa kana cikin raunin murya yace. “A.J”. Cikin sauri da zaƙuwa Moddibo yace. “J ina kake?”. Girgiza kai M Jameel Yayi tare da cewa. “A.J ban san inda nake ba ina Ummina!?”. Runtse Idanu Moddibo yayi tare da taune lips ɗinsa kana yace. “Tana lafiya J?”. Cikin sanyin Murya M Jameel yace. “J ka tabbata?”. Cikin raunatacciyar murya yace. “Na'am”. jin haka yasa yaci gaba da cewa. “Kace mata kada tayi kuka tayi ta min. Addu'a A.J ina sonka Ina son Ummina Ina son Abbana Ina Son Asma'u Ina son Bashir”. Da sauri Moddibo ya dafe ƙirjinsa dake harbawa da masifan ƙarfi cikin raunin murya M Jameel ya cigaba da cewa. “A.J Ina son Khausar tashigo rayuwar mu”. Cikin tsanananin rauni Moddibo yace. “Na sani J nasan kana son mu muma muna sonka, kuma in sha Allah duk zamu kasance a tare, zata shiga rayuwarka J zan mutunta abinda kakeso J”. Girgiza kai M Jameel Yayi still cikin raunin murya yace. “Ngd A.J in kayi haka kayi min komai, kayiwa Ummina magana idan akwai wani abu a hannunta ta bayar ahaɗa azo a karɓeni awajen nan dan Allah katemaka min”. Araunane Moddibo yace. “Insha Allah J zan taimaka da duk kan iyawa ta da kuma duk kan damata J koda ace da raina ne zan fanshi ranka da rayuwarka Insha Allah zamu fito da kai”. Jinjina kai M Jameel yayi tare da faɗin. “Nagode Nagode A.J ina maka fatan al'khairi acikin rayuwarka ga Amanar Ummina, Asma'u, Bashir,Abba da.... ka kula dasu kafin in dawo sannan kada ka mance batun Kh”... Fisge wayar akayi daga kunnensa tare da katsewa. Dafe kai Moddibo yayi cikin wani irin azabebben rauni ya fashe da matsanancin kuka tare da miƙewa batare da yace komai da Abba ba ya fice yana fita ya shiga motarsa tare dayi mata key. Kana ya ciro wayarsa tare da dearling number Ummi tana ɗagawa murya a raunace yace. “Ummi”. Cikin sanyin murya tace. “Na'am”. Cikin ƙoƙarin hana kansa kuka yace. “Ummi munyi waya da J yanzu”. Ajiyar zuciya Ummi ta sauƙe kana tace. “Dagaske Babana?”. Kai ya gyaɗa kamar tana gabansa. Cike da tsoro Ummi tace. “Babana to Meyesa kake kuka?”. Fashewa yayi da kuka kana cikin sheshsheƙa yace. “Ummi ina kukan rashin J akusa dani ne Ummi wanda suka sai motarki Alhj Abdallah kice ya tura Azo aɗauki motocina da na J duka azo asiya ahaɗa kudin duka”. Numfashi Ummi ta fesar tare da rintse idanunta kana tace. “Sunƙi ragewa ko?”. Girgiza kai yayi tare da cewa. “A'a Ummi sun rage mana Million hamsin akai yanzu ya zama Million ɗari da hamsin suke buƙata”. Ajiyar zuciya Ummi ta sauƙe tare da cewa. “Toh Alhamdulillah wataƙila zamu iya cin nasara". Cike da rauni Moddibo yace. “Insha Allah Ummi da izinin Ubangiji”. Ya faɗa tare da katse kiran jin wani kuka na neman kufce masa. Kai tsaye hanyar gida ya nufa ba abinda ke yawo acikin kunnensa face sautin Muryar J ɗinsa yana isa gida yayi Parking tare da rufe musu gate. Kai tsaye sashen Innayi ya nufa yana isa ya zauna abakin baranda tare da riƙe kansa da hannu duka biyu, Kana ya fashe da wani irin kuka mai masifar ciwo a zuciya. Wani irin azaban zogi yaji zuciyarsa na masa hadi da zafi da raɗaɗi yayin da wani masifaffen rauni ya lulluɓesa. Innayi da bacci ya fara fisgarta ne, ta miƙe da sauri jin kamar sheshsheƙan Kukan Moddibo kana ta fito tare da Kallonsa yayin da gaba ɗaya ilahirin jikinta ya ɗauki rawa cikin sanyin murya tace. “Ya dai Moddibo lafiya kuwa mai ya faru da Jameelu?”. Cikin matsanancin kuka yace. “Innayi ya zamuyi taya zanyi in. Samu in taimaki J duk kan tattalina ya ƙare babu abinda zan samu in saida cikin gaggawa. Zan saida tsohuwar motar da kika siya min da wannan sabuwar da kuma na J duka za'a siyar sannan Innayi nasan koda an siyar dasu duka, kuɗin ba zasu ciki Million ɗari ba”. Sai kuma ya kife kansa bisa guiwowinsa ya sake fashewa da sabon kuka kana yace. “Innayi sunce idan muka sake neman ragi akan kuɗin kamar mun nemi akashe J ne”,. Jingina kansa yayi jikin fillan dake gefenta tare da fashewa da matsanancin kuka hadda sheshsheƙa. Cikin Sanyin jiki Innayi ta zauna kusa dashi batare da tace yayi shiri ko kuma ya daina kukan ba, domin ta tabbata duk abinda yasa Moddibo kuka ba ƙaramin abu bane, kana idan har bai yiwa wannan abin kuka ba to mai zai yiwa kuka arayuwarsa. Moddibo kuwa kuka ya cigaba da yi tamkar ransa zai fita har shidewa yake. A ƙalla ya ɗauki Mintuna masu tsawo yana kuka kafin ahankali ya ɗago kansa tare da kallon Innayi kana yace. “Innayi”. Cikin sanyin murya tace. “Na'am Moddibo”. Cikin Muryansa daya dishe da kuka yace. “Innayi ta wace hanya ce wace damace wane daliline kike samu kike mana duk kan buƙatun rayuwarmu? Innayi in dai har adana kuɗi kikayi in dai har basu ƙare ba Innayi ki fito mana dasu ki taimakeni aceci J dashi”. Jinjina kai tayi kana tace. “Moddibo gaba ɗaya tattalin da mukayi na zaman rayuwar mu awannan yanki awannan gari a wannan ƙasar anje matakin da gaba ɗaya tattalin namu yazo ƙarshe sabida lokacin komawa muhalli ya kusan cimmmana”. Sai kuma ta kalli Moddibo da har zuwa lokacin hawaye ke bin Fuskarsa kana tace. “Na tanadi komai ne domin sanin cewa muna da bukatar su kama daga karuntaka, ci, sha, Jinya, sutura. Da dai sauransu to yanzu kuma lokaci ya tafi rayuwa ta juya abubuwa sun tafi baki ɗaya tattalin namu yayi ƙasa tsadan rayuwa ya cinye kaso mafi tsoka”. Numfashi Moddibo ya fesar kana yace. “Innayi koma wani irin tattaline shin babu ragowa ne ko kaɗan ne?”. Kai ta gyaɗa tare da cewa. “Akwai ragowa”. Cikin kuka yace. “Menene amfanin ragowan duk tattalin arzikin da kike dashi matukar dai ba zai fito atemaki J ɗina da shiba Jamelunki fa ya fito daga inda yake fa”. Ya ƙare mgnar cikin ƙunan rai, domin gani yake kamar ma duk duniya ba'a damu da J ɗinsa ba. Ita kuwa Innayi cikin tafiya wani sashi nazarin Jinjina kai tayi tare da cewa. “Bashi da amfani Indai bazan fito dashi ba, amma bari na fito dashi amma yanzu ka fara yin shiru tukunna kana kayi min al'ƙawarin cewa bazaka tambayeni komaiba akan duk abinda zaka gani”. Kai ya gyaɗa mata kana yace. “Innayi muga abinda zan fara samu awajenki tu kunna zanfi jin sanyi, ni yanzu a duniya babu tambayar da ke bakina daya wuce ina J yake , wanne hali yake ciki”. Sai kuma ya fesar da zazzafan numfashi tare da cewa. “Wallahi Allah ji nakeyi tamkar naje na zauna abakin masallacai inyita bara asamu ahaɗa kudi in cikata in karɓo J Innayi ya zanyi”. Cike da rauni Innayi tace. “Ba zakayi bara ba Moddibo Bari muga abinda Allah zai mana”. Kai ta gyaɗa tare da jan hannunsa suka nufi bayan ɗakinta inda randunan ƙasa ke ajiye. Kallon Moddibo da har zuwa lokacin hawaye ke zuba a idanunsa tayi kana tace ɗaga min randan nan”. Sauri kallonta yayi kana ya Kalli randan ƙasan tare da cewa. “In ɗaga miki randa kuma?”. Ba tare data kallesa ba tace. “Kada kayi min musu idan na baka Umarni kabi”. Kai ya gyaɗa cikin sanyin yace. “Toh”. Tare da ɗaga randan ya matsar gefe. Ajiyar zuciya ta sauƙe kana tace. “Toh ɗaga fantekar”. Kai ya ɗaga tare da matsar da fantekar dake cike da ƙasa gefe. Yana janye fantekar yaga ƙasan wajen alailaye. Ahankali Innayi ta zauna agaban wajen Moddibo kuwa cikin sanyi jiki ya durƙusa agefenta. Itako Innayi hannunta ta sanya ta fara tono ƙasan dake wajen ganin duhu agarin yasa Moddibo sanya hannunsa acikin aljihu ya ciro wayarsa tare da kunna tochligt ya haska mata inda take tonawan. Innayi kuwa ahankali ta cigaba da tono ƙasan bayan ta gama kwashe ƙasan ya rage sauran wasu manyan duwatsu ahankali ta ciresu duka. Cike da mmki Moddibo ya tsaida idanunsa akan fafakekken rami an lailayeshi da siminti yana rufe da murfin tukunya kamar na lamba uku, da ɗan ƙarfi ta ɗago Murfin tukunya. Cikin sauri Moddibo yayi saurin rintse idanunsa da karfu sakamakon wani haskene mai masifar sheƙi daya ɗauke masa idanu daya kashe masa idanu, A hankali ya kuma saƙe buɗe inadunsa, da sauri ya mitso ganin yadda cikin ramin ke sheƙi da ƙelƙeli mai ɗauke ido yake fitowa daga cikin ramin, acan ƙasan ramin kuwa cike yake da ƴan ƙananan sulallan gwala-gwalai wanda basu fiye yawa ba sosai hasken ya ɗauke masa idanu saboda hasken wayarsa daya haske cike da tsanananin mamakin ya sunkuyo tare haska cikin ramin da kyau kana ya sanya tafin hannunsa acikin ramin ya ɗebo guda huɗu tabbas sulallan Gwalne...! Littafin SAKAYYAH na kuɗine ko kin ganshi a wani wurin na satane. Ki biya ki karanta cikin Aminci 1k ne kacal 0661110170 GTBank AISHA ALIYU GARKUWA. By *GARKUWAR MARUBUTA* [30/07, 1:42 PM] Halimatu A/rahman Sadeeya: *Littafin nan dai ba free book bane, na kuɗine ko kin gashi a wasu wuraren da ba Group na da ake biya insa mutum, littafin 1k ne kacal in sha Allah zaki karanta shi daga forko har ƙarshe akan 1k kacal 0661110170 GTBank AISHA ALIYU GARKUWA sai ki turo min shaidar biyanki ta WHATSAPP 09097853276 ki biya ki karanta cikin Aminci da salama babu haƙƙin kowa a kanki yar uwa* Sbpndegoo. Lamiɗo kuwa cikin yanayin, tausayi da jinƙai da ƙauna mai haɗe da taraddadi da tsoro, ya sanya tafin hannunsa na dama ya tallafo, fuskar Ramadan ya juya gefe da gefe ga mmkinsa gaba ɗaya uwayan yaron ya koma lagob-lagob cikin yanayi da kiya da son aro Jarumtaka ya runtse Idanunsa tare da maimaita kalmar Hasbunallahu wani'imal wakil. Innalillahi wa'inna ilahi rajiu'n. Cikin sauri Hajiya Bunayya dake zaune ta buga hannunta aƙirji tare da kallon Lamiɗo daya zubawa Ramadan ido tace. “Mai Martaba ya rasu ko?”. Ajiyar zuciya ya sauƙe tare da ɗago ido ya kalleta kai ya girgiza mata batare da yace komai ba. Da sauri Mommy dake tsaye tayi baya tare da zama da ɓas akan kujeran dake bayanta, baki ɗaya jikinta ya saki Atake ta fara Maimaita kalmar. “Innalillahi wa'inna ilahi rajiu'n Hasbunallahu wani'imal wakin”,ta faɗa hawaye na bin kuncinta Shar-shar. Khausar kuwa juyawa tayi ta kalli Hajiya Bunayya kana ta mayar da kanta kan Mommy da hawaye ke bin kuncinta ahankali ta sake maida kallonta kan Lamiɗo da yayi shiru yana jan yatsun Ramadan alamar yana dai-dai-tasu. Cikin wani irin yanayi tace. “Abba mu tafi dashi asibiti,Abba mu kaisa asibiti”. Jujjuya kai Lamiɗo yayi kana yace. “Khausar ki nutsu”. Kallon Hajiya Bunayya da Idanunta ke kan Ramadan yayi yace. “Hajiya Bunayya kama khausar ki zaunar da ita”. Mommy kam tana zaune akan kushin babu abinda take maimaitawa face kalmar Innalillahi still hawaye na bin kuncinta. Ganin haka yasa Lamiɗo fesar da numfashi kana ya miƙe tare da ɗaukar Ramadan awuyansa ya fice. Da sauri Khausar ta miƙe tare da bin bayansa tana cewa. “Abba inzo mu tafi Asibitin ne!?”. Tsintsiyar hannunta Hajiya Bunayya ta riƙe tare da gyara zamanta tace. “Khausar ki nutsu mana ki dawo ki zauna?”. Kai khausar ta girgiza cikin rawan murya tace. “Ki sake ni zamu tafi asibiti ne kiga Ramadan fa”. Jinjina kai Hajiya Bunayya tayi tare da faɗin. “Ki zauna mana ba kiji Abbanku yace ki zauna ba. Kai ta gyaɗa cikin wani irin yanayi ta koma ta zauna. Lamiɗo kuwa yana fita kai tsaye sashen Gimbiya Dadu ya shiga bakinsa ɗauke da Sallama zaune ya samu Gimbiya Dadu afalon. Ganinsa Rungume da Ramadan yasa cikin sauri tace. “Ya dai lafiya Lamiɗo meke faruwa?”. Cikin sanyin murya yace. “Ramadan ne fa ki duba min shi”. Kai ta gyaɗa tare da Matsawa gaban Ramadan dake kwance ƙasan ɗakin yatsunta biyu ta kai saitin hancinsa sannan ta riƙe jijiya hannunsa kallon Lamiɗo tayi cike da mamaki tace. “Ha'a bashi da rai ai ajikinsa?”. Araunane Lamiɗo ya ɗago idanunsa da suka kaɗa sukayi jawur jijiyoyin kansa ya tashi cikin raunin murya yace. “Nima dai kamar haka na gani ahannuna na ya cika kamar babu rai atare da shi. Jinjina kai Gimbiya Dadu tayi cikin rawan murya tace. “Tabbas ba Rai atare dashi Ramadan ya rasu fa”. Ta ida maganar tare da ɗago hannunsa ta juya sangalam duk ta inda ta juya sai ya tafi luuuu zai fadi kana ga bakinsa dake aɗan buɗe idanua kafe. Ahankali Lamiɗo ya sunkuyar da kansa akan Ramadan hawaye masu ɗumin gaske suka shiga zubo masa asaman kincinsa, suna ɗiga kan fuskar Ramadan tal-tal yayinda jinkinsa ya shiga tsuma. Gimbiya Dadu kuwa bayanta ta jingina da jikin kujeran cikin sanyin murya tace. “Allah sarki Ramadan ashe dai ciwon kan nan na ɗauka ne? Ciwo lokaci ɗaya!?”. Akuma dai-dai lokacin Uncle Naseer ya shigo falon ganin yanayin da suke ciki ne yasa ya zauna gefen Gimbiya Dadu tare da cewa. “A Lafiya meke faruwa?”. Ahankali Gimbiya Dadu ta ɗago kai tare da Kallonsa tace. “Wallahi Ramadan ne Allah ya masa rasuwa!”. Arazane Uncle Naseer ya Kalli Gimbiya Dadu tare da kallon Ramadan dake kwance cikin wani irin yanayi yace. “Ha'a wani irin magana ne Gimbiya Dadu ya zakice Ramadan ya rasu!? Ko ke Dr ce ya za ayi kice ya rasu taya kika gane hakan?”. Kallonsa ya mayar kan Lamiɗo daya zubawa Ramadan ido kana yace. “Yah Lamiɗo mu kaisa asibiti”. Kallonsa Lamiɗo yayi tare da Girgiza masa kai still Idanunsa na nan ja jawur ruwan hawaye na kwance acikinsu yayinda jikinsa ke cigaba da tsuma zuciyarsa na harbawa da masifan ƙarfi. Uncle Naseer kuwa hannu yasa a aljihu tare da ciro wayarsa yayi dearling number family Dr su yana ɗagawa yace dan Allah yazo ya duba yaro agida Dr ya amsa da toh. Bayan minti 16 minute Dr yazo bayan ya duba ya tabbatar musu da Ramadan ya rasu kimanin minti talatin da suka wuce. Sai asannan Uncle Naseer ya yarda kana ya raka Dr ya tafi yana dawowa. Sashen Gimbiya Dadu ya hadu da Lamiɗo ya fito da Ramadan Rungume akafaɗarsa bayansa yabi Lamiɗo kuwa kai tsaye Falonsa ya nufa yana shiga ya kwantar da gawar Ramadan Atsakiyar ɗakin kana ya cire masa suturar jikinsa ɗen oh foɗimo. Cikin rauni da tsinkewar zuciya ya nufi ɗakin Mommy a inda yabar Mommy zaune anan ya dawo ya sameta still Idanunta na zubar da hawaye masu zafi da ƙuna a zuciya. Khausar dake gefenta ta kalleta tare da cewa. “Mommy Meye faru me yasamu Ramadan?”. Ahankali Mommy ta janyota jikinta tare da kwantar da ita akan cinyarta kana ta sanya hannunta akanta tana shafawa cikin sanyin murya mai cike da rauni tace. “Khausar muyi haƙuri Ramadan kam ya tafi ya barmu. Ubangiji Allah yajiƙan sa Allah ya masa rahma Allah yasa mai cetone”. Cikin tsananin tashin hankali Khausar ta fashe da matsanancin kuka me tsuma zuciya yayin da ta shiga girgiza kanta kallon Mommy tayi Muryanta na rawa tace. “Mommy Ramadan kike cewa ya rasu!? Mommy wannan wani irin magana ne!? Dan Allah Mommy kice mafarki nake Mommy kice ba gaskiya bane!”. Girgiza kai Mommy tayi still Hawaye na bin fuskarta amma ta gaza furta komai. Cikin sauri Khausar ta toshe bakinta jin wani matsanancin kuka ya taho mata. Ajiyar zuciya Lamiɗo ya sauƙe tare da ƙarasawa cikin falon ya zauna kusa da Mommy, kasancewar akan 3sitter take. Cikin sanyi murya yace. “Khausar kiyi haƙuri kinji ko?”. Kallonsa tayi da jikaƙƙun Idanunta kana tace. “Abba da gaske wai Ramadan ya rasu!?”. Nunfashi Abba ya fesar tare da jinjina mata kai yace. “Da gaske ne Khausar ya muka iya da hukunci Ubangiji, dama shi ya bamu Ramadan kuma shi ya karɓesa, kiyi haƙuri ki daina kukan nan kinji ko!?”. Girgiza kai tayi tare da sake fashewa da matsanancin kuka mai gunji. Dafa kanta Lamiɗo yayi cike da tausayawa yace. “Kiyi haƙuri yanzu ma Naseer ya kira Dr yazo ya dubasa sannan ya tabbatar min da cewa ya rasu!”. Cikin wani irin yanayi mai cike da ruɗu Khausar ta miƙe da gudu tare da shiga Bedroom ɗinta ta faɗa kan gado tare da sakin marayan kuka. Lamiɗo kuwa bayan ya sake rarrashin Mommy tare da bata haƙuri da kuma nuna mata muhimmanci tawakkali da haƙuri ya mike ya fita. Bayan angama shirya Ramadan an masa wanka an suturtasa yanda addinin Musulunci ya tsara aka kaisa gidansa na gaskiya. Bayan andawo Lamiɗo da ƴan Uwansa da kuma Abokan arziƙi aka zauna zaman Makoki. Wunin wannan ranan haka Mommy da Khausar suka yini cikin alhini da jimamin rashin Ramadan Hajiya Bunayya kuwa sosai tayi farin ciki sai dai kallo ɗaya zaka mata ka fuskanci mutuwar ta shigeta domin ayanda take nunawa tafi Mommy damuwa wani abin ma Mommy ke tausarta tana bata haƙuri. Washe gari Khausar ce zaune a ƙasa Mommy na Kan kujera gabansu Kuma kayan Breakfast ne. Cikin sanyin murya Mommy ta kalli Khausar tare da cewa. “Khausar ki matso kici abinci”. Girgiza kai Khausar tayi tare da kallon Mommy da kumburarrun Idanunta kana cikin sanyin murya tace. “Mommy ba najin yunwa”. Ajiyar zuciya Mommy ta sauƙe tare da rintse Idanunta kana tace. “Khausar ki matso kici abinci bana son haka zamuyi fushi da abinda Ubangiji ya jarabcemu da shine Allah daya halicci Ramadan yafimu son sa shi ya bamu Ramadan kuma shi ya ɗauke mana shi!”. Wasu hawaye masu masifar zafi ne suka zubowa Khausar akuncinta cikin matsanancin kuka tace. “Mommy shikenan!, Shikenan Ramadan ya tafi baza mu sake Kallonsa ba shikenan mun ransa shi har abada. Innalillahi wa'inna ilahi rajiu'n”. Kallonta Mommy tayi still Idanunta cike da ruwan hawaye Akuma dai-dai lokacin wayarta ya ɗauki ruri. Kallon screen ɗin wayar tayi nan taga sunan Hajja Nana na yawo. Cike da ladabi tayi Picking tare da kaiwa kunnenta tace. “Hajja ina yini?”. Daga ɗaya ɓangaren Hajja Nana tace. “Lafiya lau ina Khausar!?”. Cikin sanyin murya Mommy ta kalli Khausar da hawaye ke zuba a Idanunta kana tace. “Gata nan”, “Toh ki bata wayar”, cewar Hajja Nana ta. Kai Mommy ta gyaɗa tare da miƙawa Khausar wayar. Amsa Khausar tayi cikin Muryan kuka tayi sallama. Cike da kulawa Hajja Nana tace. “Ke kuma lafiya ya naji muryanki haka kukan me kike!?”. Cikin sheshsheƙan kuka Khausar tace. “Hajja Nana Ramadan ɗin mune ya rasu”. Hajja Nana kuwa cikin sauri tace. “Innalillahi Wa'inna Ilahi rajiu'n Ayyah Allah sarki Ubangiji Allah ya jiƙansa da rahma Allah yasa maicetone ai bamu da labari bamu sani ba bawa Mommy naki”. Kai Khausar ta gyaɗa tare da miƙewa Mommy wayar. Jin Mommy ta amshi wayar yasa Hajja Nana cewa. “Wai ashe Ramadan ya rasu!?”. Kai Mommy ta gyaɗa kana cikin sanyin murya tace. “Eh Wlh”. Ajiyar zuciya Hajja Nana ta sauke tare da cewa. “Ikon Allah Meye sameshi haka?”. Numfashi Mommy ta fesar tare da gyara zaman ta kana tace. “Wallahi ciwon kai ne mako ɗaya”. Cikin sanyin murya da tausayawa Hajja Nana tace. “Allah sarki Allah ya gafarta masa Ubangiji yasa maicetone! Dama yanzu Malam Liman zai shigo Gembulan Insha Allah zan biyo shi muzo”. Jinjina kai Mommy tayi cikin sanyin murya tace. “Toh Allah ya kawo ku Lafiya mungode sosai”. Bayan Mommy ta kashe wayar ta kalli Khausar data zubawa kayan Breakfast Ido Cike da tausayawa ta shiga lallashinta. Acan gidan Ummi kuwa Moddibo ne zaune afalon ya tsurawa waje ɗaya Idanu yayin da Ummi kanta ke ƙasa hawaye zira-zira baki ɗayan sun zurfafa acikin tunanin da suke Asma'u ta fito daga kitchen cikin mutuwar jiki ta tsugunna kusa da Ummi kana cikin sanyin murya tace. “Ummi”. Ahankali Ummi ta ɗago Idanunta dake zubar da hawaye kana cikin sanyin murya tace. “Na'am”. Lumshe idanu Asma'u tayi tare da faɗin. “Ummi yanzun nan mukayi waya da Khausar tace in gaisheki”. Kai Ummi ta gyaɗa cikin sanyin murya tace. “Ina Amsawa”. Asma'u kuwa cikin raunin murya tace. “Ummi wai Ramadan ya rasu fa”. Cikin sauri Ummi ta ɗago kanta dake ƙasa ta kalli Asma'u shima Moddibo cikin sauri ya kalli Asma'u zuciyarsa na cigaba da bugawa da masifar ƙarfi. Ajiyar zuciya Ummi ta sauƙe cikin raunin murya tace. “Innalillahi wa'inna ilahi rajiu'n yaushe ya rasu!?”. Gyara zama Asma'u tayi cikin sanyin murya tace. “Shekaran jiya fa take cemin randa tazo bayan ta koma ciwon kan ya fara mishi, sunyi ta sintirin asibiti a banza, tace shekaran jiya kuma haka aka kwana dashi haka jiya da Asbah ma ya tashi dashi washe gari da safe bayan sallar Asbah ya rasu sai bayan Azahar akayi jana'izar sa!”. Girgiza kai Ummi tayi tare da fesar da numfashi kana tace. “Allah sarki rayuwa Ayyah Aysha ta ɗanɗani Mutuwa mai zafi da raɗaɗi mutuwar ɗa akwai ciwo Allah ya masa rahma Allah yasa maicetone”. Cikin sanyin murya Asma'u tace. “Ameen Ummi”. Jinjina kai Ummi tayi tare da cewa. “Insha Allahu zanyi ƙoƙari muje”. Moddibo kuwa ahankali ya buɗe Idanunsa dake lumshe ya kalli Ummi tare da cewa. “Allah yajiƙan sa da rahma, shine yaron da Mota ya buge ko?”. Kai Asma'u ta gyada tere da cewa. “Eh shine”. Cije lip ɗinsa na ƙasa yayi tare da cewa. “Allah sarki kwanansa na gaba alokacin Allah ya gafarta masa”. Cikin sanyi murya Ummi tace. “Ameen”. Ajiyar zuciya Moddibo ya sauƙe kana yace. “Ummi bari in tashi Inje wajen Abba naji ya ake ciki muji daga Jiya zuwa yau ko sun kira”. Kai ta gyaɗa tare da cewa. “Toh shikenan”. Cikin sanyin jiki ya miƙe tare da ficewa kai tsaye gidan Abba ya nufa. Bayan ya isa gidan ya shiga falon Abba nan ya samu Dr Muktar zaune zama gefen Abba yayi bayan sun gaisa Moddibo ya sauƙe numfashi kana cikin sanyin murya yace. “Abba har yanzu basu kira ba”. Kai Abba ya gyaɗa masa tare da rintse Idanunsa kana yace. “Basu kira ba Aliyu bansan me mutanen nan suke nufi da muba”. Tagumi Moddibo da Abba sukayi duk sunyi jugum-jugum dasu. Misalin ƙarfe biyu da rabi na rana Hajja Nana da Malam Liman suka iso gidan Lamiɗo bayan sun gama gaishe-gaishe suka zauna har aka Idar da La'asar Lamiɗo ya shigo tare da kallon Hajja Nana kana yace. “Hajia ki fito malam Liman yana jiranki”. Kai ta gyaɗa tare da cewa. “Toh gani nan fitowa”. Kallonta ta mayar kan Mommy dake jan Carbi kana tace. “Yanzu kam ba abinda zance miki, ta'aziyya muka zo miki amma Insha Allah kwanan nan zan dawo kan batun Khausar”. Jinjina kai Mommy tayi tare da cewa. “Toh shikenan Nagode Hajja Nana Allah ya saka da alkhairi”. Miƙewa Khausar tayi tare da bin bayan Hajja Nana jikinta sanye da dogon hijabi har ƙasa yayin da hannunta ke riƙe da wayarta Idanunta sunyi luhu-luhu dasu suna fita coumpund ɗin taga Malam Liman acikin mota amazaunin Driver. Wara kumburarrun Idanunta tayi kana cikin sanyin murya tace. “Iyeee lallema tsohon nan ashe ka iya mota?”. Murmushi malam Liman yayi tare da gyada mata kai kana yace. “Eyyy sosai ma kuwa dama lokacin da kikaje ai mota ta talalace ne shiyasa ankaita wajen gyara to wata aka sake siya min”. Murmushi tayi kana tace. “Ashe kunji daɗi ƙauyenku akwai mota”. Jinjina kai yayi da murmushi afuskarsa yace. “Hadda ke ai acikin ƙauyen ya zaki cire kanki?”. murmushi tayi cikin yanayin sanyin tace. “ai Lallai dai kam to Allah ya tsare muku hanya”. Ta faɗa tare da komawa cikin falon Ummi. Kallon Hajja Nana Malam Liman yayi bayan ya dai-dai-ta motar akan kwalta yace. “Addah Nana za muje gidan Malam Arɗo wannan ɗaliban nawa”. Kai ta gyaɗa tare da cewa. “Toh ba matsala muje mana”. Jinina kai Malam Liman. bayan sun isa gidan malam Arɗo yayi Parking tare da isa falon baƙinsa wanda ke harabar gidan bakinsu ɗauke da Sallama. Daga ciki malam Arɗo wanda ke zaune tare da Moddibo ya amsa tare da basu Izinin shiga. Bayan angama gaishe-gaishe Malam Arɗo yace. “Lafiya Malam Liman yau ziyarar yamma”. Cikin jimami Malam Liman yace. “Wallahi ɗan gidan Mai martaba Lamiɗo ne ya rasu shine muka zo Ta'aziyya”. Jinjina kai Malam Arɗo yayi tare da faɗin. “Bashakka hakane ai yaron ɗalibin mune, wallahi ni lokacin da akayi jana'izar nasa banji ba amma Insha Allah zanje ta'aziyya da izinin Ubangiji”. Kai Malam Liman ya gyaɗa tare da gyara zamansa kana yace. “Wallahi kuwa rasuwa abin tausayi wai ciwo dare ɗaya ya tsananta”. Girgiza kai Malam Arɗo yayi da alamun damuwa atare dashi yace. “Ayyah haka fa kwanaki mota ta bigeshi abakin Makarantar mu fa. Yaron ya samu karaya wannan bugewan ba wanda yayi tunanin zai warke Allah sarki ashe ajalin nakusa”. Kai Hajja Nana ta gyaɗa tare da cewa. “Haka fa rayuwar take ciwon Ajali lokacin ɗaya zai shige mutum sai dai kaji ance babu shi saidai fatan Allah yasa mu cika da Imani”. Baki daya suka amsa da Ameen banda Moddibo daya zubawa ƙasan ɗakin Idanu da alama ya zurfafa acikin tunanin da yake. Ahankali Malam Liman ya juya tare da kallon Moddibo kana ya maida kallonsa kan Malam Arɗo tare da cewa. “A'a Malam Arɗo wannan jikan namu dashi kaje kwanakin baya ko?”. Kai Malam Arɗo ya gyaɗa tare da kallon Moddibo da har zuwa lokacin kansa ke ƙasa yace. “Eh jika nane kuma Malamine Amakaranta na”. Murmushi Malam Liman yayi tare da faɗin. “Ayyah Masha Allah Yayi kyau amma lafiya na ganshi haka baki ɗaya ya canza ko bada shine ku kaje Jauro yaya kwana kiba”. Cikin sanyi malam Arɗo ya gyaɗa kai kana yace. “Eh da shine mukaje”. Cike da mamaki Malam Liman yace. “Amma lafiya kuwa?”. Numfashi Malam Arɗo ya fesar tare da Girgiza kai kana yace. “Ina kuwa lafiya wannan zamani da Allah ya kawo ku. Malam Liman kai dai Ubangiji ya rufa mana asiri”. Anutse Malam Liman ya gyara Alkyabbar dake jikinsa kana yace. “Amin ya Allah". Kana ya ɗaura da cewa. “Amman Meke faruwa?”. Gyara zama Malam Arɗo yayi tare da fuskantar Malam Liman cikin sanyin murya yace. “Akwai wani Amininsa Yaron Alhj Bashir mai Dala Jameelu da aka sace baki ɗaya abin ya fitar mana hayyaci mun rasa wani irin tunani zamuyi ma acikin wannan al'amari”. Cikin sauri Malam Liman yace. “Sunhanallah”. Cike da damuwa Malam Arɗo ya gyara zama tare da zayyane musu duk abinda ke tafiya yanda aka sacesa da kuma yanda akanemi kuɗin fansa kana da yanda suka daina jin labarinsa kwata kwata. Girgiza kai Malam Liman yayi kana yace. “Subhanallah”. Ya faɗa tare da maida kallonsa kan Moddibo wanda shima adai-dai lokacin ya ɗago Idanunsa da suka kaɗa sukayi jawur baki ɗaya fuskarsa tayi fayau ya rame. Cike da tausayawa Malam Liman yace. “Amma yanzu baku da labarin sa!?”. Girgiza kai Moddibo yayi kana cikin raunin murya yace. “A'a bamu da labarinsa yau kusan kwana goma sha biyu kenan bamu da labarinsa, sannan wayarsa bata shiga suma kuma sun daina kiran mu abinda yafi komai tayar mana da hankali kenan, bamusan Inda J yake ba”. Malam Liman kuwa Anutse ya fesar da nunfashi cike da tausayinsa kana ya gyara zamansa tare da cewa. “Bakomai Insha Allah za muyi addu'a da izinin Ubangiji duk inda yake a faɗin duniyar nan Ubangiji zai bayyana shi”. Kai Moddibo ya gyaɗa tare da Gyara zamansa Malam Liman ya cigaba da cewa. “Da Iznin Ubangiji Allah zaiyi dalilin da za'a ganshi zan baka addu'a'o'in idan har zaku jure kuyita yi da kai da mahaifiyarsa da kuma Mahaifinsa, to za ayi nasara kuma nima zan tayaku”. Cikin sauri Moddibo ya sauƙe Ajiyar zuciya tare da cewa. “Munaso Malam ai addu'a'u Saiful mu'uminun ce ita addu'a itace makamin bawa dama ita muke tayi ai”. Kai Malam Liman ya gyaɗa tare da cewa. “Toh shikenan zan baka adduo'i Insha Allah da izinin Ubangiji Allah zai bayyana shi, aduk inda yake afaɗin duniyar nan sai dai walau ko araye ko amace amma Ubangiji zai bayyana shi insha Allah za'a ga walallanilansa”. Cikin sanyi Moddibo yace. “Mun gode Malam”. Cike da nutsuwa da kamala Malam Liman ya fara bashi Adduo'i Moddibo kuwa cikin sauri ya ɗauki jotter da biro ya fara rubutawa wasu da yawa daga cikin Adduo'in Moddibo ya sansu wasu kuma baisan suba sabida shi ilimi kogine faɗi gareshi. sosai ya riƙa faɗa masa adduo'in Moddibo kuwa yana rubuta adduo'in yana bitar su yasan da izinin Ubangiji idan ya zauna na awa biyu yayi research ɗinsu zai haddace su. Bayan Malam Liman ya gama bawa Moddibo adduo'in Hajja Nana ta saki ajiyar zuciya kana tace. “Toh Ubangiji Allah ya karesa Allah ya bayyana sa aduk inda yake”. Cikin sanyi murya suka amsa da Ameen. Kallon Malam Liman Hajja Nana tayi tare da faɗin. “Ai wannan Jikanmu ne ka tuna ƙawata Innare?”. Kai Malam Liman ya gyaɗa mata tare da cewa. “jikanta ne?”. Jinjina kai Hajja Nana tayi tace. “Eh shine”. Murmushi Malam Liman yayi tare da faɗin. “A Masha Allah Yayi kyau”. Ita kuwa maida kallonta kan Moddibo tayi wanda gaba ɗaya ya zubawa takardan adduo'in ido kana tace. “Idan ka koma ka gaishe min da ita yau kam bazan samu zuwa ba yanzu ma munyi yamma”. Kai ya gyaɗa kana cikin sanyin murya yace. “Toh mun gode Allah ya saka da al'khairi Insha Allah zataji”. Miƙewa Hajja Nana da Malam Liman sukayi tare da yi musu Sallama suka tafi Moddibo kuwa yana fita daga gidan Malam Arɗo kai tsaye gidan Abba ya wuce Bayan sun gaisa Abba yayi shiru tare da tsirawa waje ɗaya ido gabansa da magunguna da alamar bai daɗe da gama shaba. Ahankali Abba ya maida kallonsa kan Moddibo da yaga yayi mugun rama ya sake zama wani so silent duk da dama can bamai yawan magana bane amma yanzu shirun yayi yawa. Ajiyar zuciya Abba ya sauƙe tare da faɗin. “Aliyu kaga yanda ka koma kuwa ka dawo kamar wanda yayi shekara yana jinya”. Kallon Abba Moddibo yayi tare da sakin murmushin da yafi kuka ciwo kana ya sunkuyar da kansa ƙasa tare da cewa. “Abba”. Still Idanun Abba na kansa yace. “Na'am”. Ajiyar zuciya Moddibo ya sauƙe kana yace. “Insha Allah Abba inaji Ajikina J ɗina ya kusa bayyana”. Numfashi Abba ya fesar tare da sakin murmushi na alamar jin daɗi kana yace. “Allah yasa haka Aliyu”. Ahankali Moddibo ya amsa da Ameen kana yace. “Abba ya zun nan akwai wani malami da muka haɗu dashi agidan malam Arɗo ko Malam Arɗo da kansa wajensa yake zuwa ɗaukan darasi ya bani adduo'i masu tarin yawa”. Sai kuma ya lumshe idanunsa tare da cije Lip ɗin sa na ƙasa kana yace. “Adduo'in da nake ji ajikina insha Allah Ubangiji zai amsa mana, gashi ya bani adduo'i da dama yace mu riƙa yi dani da kai da Ummi. Insha Allah duk inda J yake afaɗin duniya Allah zai bayyana mana shi za muji labarinsa aduk inda yake”. Murmushi Abba yayi tare da faɗin. “Mungode ƙwarai Allah yasa adace”. “Ameen yace kana yaci gaba da cewa. “Kyansa ma mu ƙara harda Azumi amma dama Ni tuntuni ina Azumin Abba kaima ka gwadayi. In Sha Allah ni zan shiga itiƙafi na tsawon kwanaki uku Insha Allah”. Kai Abba ya gyaɗa kana yace. “Toh shikenan Moddibo Allah ya temaka” Nan Moddibo ya bawa Abba adduo'in kana ya tafi kai tsaye gidan Ummi ya nufa itama ya bata Adduo'in cikin sanyin murya tace. “Toh Babana Insha Allah zanyi”. Kai ya gyaɗa kana ya fice kai tsaye gida ya nufa yana isa sashen Innayi ya wuce sannan ya mata bayanin duk abinda ya faru tare da bata Adduo'in da Malam Liman ya bayar kana ya faɗa mata saƙon gaisuwar da ƙawarta ta bata. Kana ya gyara tsayuwar sa tare da cewa. “Toh zan shiga 'itiƙafi a ɗaki”. Jinjina kai Innayi tayi da faɗin. “Toh me dame kake bukata?”. Girgiza kai yayi kana cikin sanyin murya yace. “Bana buƙatar komai Akwai Friuts a Fridge sannan akwai kayan tea kuma azumi zanyi”. Kai ta gyaɗa tare da cewa. “Toh Allah yatemaka Allah ya bada sa'a. Ameen ya amsa tare da nufar Bedroom ɗinsa. Yana shiga yaja ƙofa ya rufe tare da nufar toilet ya ɗaura alawala yana fitowa ya zauna bisa salla ya fuskanci gabas. Ya fara rera karatun Al'ƙur'ani sai karfi ɗaya ya fara jero Adduo'i yanayi yana kuka. Sai ƙarfe uku ya kwanta ƙarfe huɗu dai-dai ya farka yasha tea da fruits Washe gari ya tashi da Uzumi haka ya yini da azumi yaita Adduo'i da karatun Alkur'ani idan dare yayi haka zaita nafilfili sai karfe uku zai kwanta ƙarfe huɗu zai tashi yayi Sahur haka ya cigaba da rayuwa har tsawon kwanaki uku aɗaki yana fadawa Ubangiji bukatarsa Aɓangaren Abba ma haka ya ɗauki tsawon kwanaki uku yana bautar Ubangiji haka Ummi ma baki ɗaya ta miƙawa Ubangiji lamuranta. Yau ya kama kwana na huɗu kenan ahankali Moddibo ya fito daga falonsa tare da tsayawa abakin farandar. Innayi dake tsaye ta zuba masa ido lokaci ɗaya taji hawaye na zubo mata ganin yanda yayi wani masifar ramewa idanunsa sunyi luhu-luhu dasu yayinda sajensa ya cika fuskarsa kasancewar gashi mai santsi da laushi yasa sai sheƙi yake fuskarsa nan tayi fayau sai sheƙi take alamun a ɗan kumbure take sabida yawan kuka da rashin isasshen bacci. Lumshe Idanu Innayi tayi hawaye masu zafi suka zubo ganin kamar daga jinya ya tashi. Moddibo kuwa ahankali ya ɗaga kai ya kalleta jin yandata tsaresa da ido. Cikin rawan murya tace. “Moddibo kaga yanda ka dawo kuwa?”. Murmushi mai ciwo yayi tare da Girgiza kansa cikin sanyin murya yace. “Innayi bari na tafi wajen Ummi”. Kai ta gyaɗa tare da cewa. “Toh baka tsaya kaci abinci ba”. Girgiza kai yayi kana yace. “A'a Innayi na ƙoshi”. Kallonsa Innayi tayi Idanunta cike da ruwan hawaye tace. “Dan Allah Moddibo ka tsaya kaci wani abu dubi yanda ka dawo fa”. Ajiyar zuciya ya sauƙe kana yace. “Toh shikenan Innayi ki bani tea”. Cikin sauri ta hado masa tea ta kawo masa karɓa yayi yasha bayan yasha ya fita kai tsaye gidan Ummi ya nufa bakinsa ɗauke da Sallama ya shiga falon. Ummi na ganinsa tayi saurin miƙewa tare da fashewa da kuka mai cike da rauni. Moddibo kuwa cikin sauri ya ƙarasa kusa da ita tare da riƙe tafin hannunta kana cikin raunin murya yace. “Ummi meyafaru Ummi kuka kuma?”. Cikin zubda hawaye ta kallesa tare da cewa. “Babana abubuwan sun haɗu sunyi min yawa acikin kwanaki Ukun nan Ba Jameelu na sannan kai ɗinma da nake gani inji sanyi na daina ganinka. Babana kaga yanda kadawo fa”. Ajiyar zuciya Moddibo ya sauƙe tare da lumshe idanunsa kana yace. “Ummi Insha Allahu in Allah ya yarda hawayen mu ya kusa daina zuba inaji Ajikina J yana kusa damu”. Numfashi ta fesar tare da cewa. “Allah yasa hakan Babana dubi yanda ka dawo fa kamar wanda aka sallamo daga asibiti kana tafiya Iska na ɗibarka”. Sai kuma ta maida kallonta kan Asma'u data zabga tagumi tana binsu da kallo baki ɗaya itama ta rame ta sake zama shiru. Cikin sanyin murya tace. “Asma'u kawo masa abinci yaci”. Kai ya Girgiza Asanyaye yace. “Ummi bana jin yunwa”. Cikin sauri da sanyi Ummi tace. “Zafa kaci abinci matuƙar kana son hankalina ya kwanta to kaci abinci Babana”. Cikin sanyi yace. “Toh Ummi”. Ahankali Asma'u ta fito hannunta riƙe da Plate ɗin dambun shinkafa dayaji Vegetables ya na fidda ƙamshi da soyayyan naman kaza akai da kwalin exotic. Agabansa ta ajiye masa kallon Ummi yayi ganin yanda ta tsare da ido tana zuba masa, ahankali ya fara cin abinci duk da yana jin cikinsa ya cushe yaci ya kai rabi kana yasha lemon Kaɗan. Ture Plate din yayi kana yace. “Ummi bari Inje gidan Abba”. Kai ta gyaɗa da fadin. “Adawo lafiya”. Moddibo na fita kai tsaye gidan Abba ya nufa yana isa ya shiga falon bakinsa ɗauke da Sallama Atare Abba da Malam Arɗo dake zaune suka amsa masa cikin sanyi Moddibo ya nufi gefen Abba ya zaune tare da Gaishe su. Kallon Moddibo Malam Arɗo yayi kana yace. “Moddibo yau kwana uku bakai babu dalilinka sannan wayarka bata shiga shine nace bari inzo tambayi Abban Jameel ko lafiya kaddai wanda suka ɗauki Jameelu ne suka ɗauke mana kai”. Ajiyar zuciya Abba ya sauƙe kana yace. “Nima da ban ganshi ba gaba ɗaya hankalina ya tashi duk da cewa nasan yana gida lafiya amma rashin ganinsa ya sake tayar min da hankalin rashin ganin Jameelu na”. Cikin sanyin murya Malam Arɗo yace. “Toh Allah ya bayyana shi Alhj Ubangiji Allah ya bayyanar dashi aduk inda yake!”. Cikin rauni Moddibo ya kalli Abba tare da cewa. “Abbah basu kira ba atsawon kwana ki ukun nan”. Girgiza kai Abba yayi da faɗin. “A'a basu kira ba Aliyu kuma ga wayar Jameelu na ta daina shiga, yanzu sannan suma sun daina kira”. Moddibo kuwa ahankali yace. “Bakomai Abba Insha Allah Allah zai bayyana shi akan al'khairi Alfarman Annabi da Alkur'ani”. Atare suka amsa da Ameen Hajiya Turai ce tashigo bakinta ɗauke da sallama bayan sun gaisa da malam Arɗo ta kalli Moddibo da faɗin. “Moddibo kwana biyu shiru gashi babu wani labarin Jameelu Ubangiji dai Allah ya bayyana mana shi”. Cikin sanyin murya suka amsa da Ameen kana ta juya ta fice. Kallon Moddibo Malam Arɗo yayi kana yace. “Moddibo muje ka rakani wani waje mana”. Kallonsa Moddibo yayi da faɗin Ni kuma?”. Kai Malam Arɗo ya gyaɗa masa kana yace. “Eh”. Girgiza kai Moddibo yayi cikin sanyin murya yace. “A'a kayi haƙuri ni kam babu inda zanje”. Kallon Moddibo Abba yayi kana yace. “Aliyu kaje ka rakasa mana”. Gyara zama Malam Arɗo yayi tare da faɗin. “Kuma ta'aziyya ne ma zai rakani, gidan Lamiɗo tunda akayi rasuwar yaron nan yau wuni na biyar kenan ban samu naje ba, kuma kaima ya kamata kaje amatsayin ka na Malaminsu”. Shiru Moddibo yayi tare da sunkuyar da kansa ƙasa. Ahankali Abba yace. “Aliyu kuje mana zama waje ɗayan nan ma bashi da daɗi”. Girgiza kai Moddibo yayi cikin sanyin murya yace. “Abba ni dai banason zuwa”. Ajiyar zuciya Abba ya sauƙe da faɗin. “Kuje mana Aliyu Ubangiji Allah yasa zuwan ya zama alkhairi”. Cikin sanyin murya yace. “Ameen”. Sannan ya miƙe Malam Arɗo na biye dashi suka fita. Acan gidan su Khausar kuwa Lamiɗo ne zaune afalon tare da wasu baƙi guda biyu da suka zo daga Taraba Alhj Ibrahim da Alhj Musa suka zo yi masa ta'aziyya sai kuma Uncle Naseer dake gefe. Mai gadi ne ya shigo bakinsa ɗauke da sallama kana yace. “Ranka ya daɗe ga Malam Arɗo da Malam Moddibo Malaman su Ramadan sunzo”. Kai Lamiɗo ya gyaɗa tare da faɗin. “A'a kace su shigo harda malam Arɗo da kansa”. Kai ya gyaɗa sannan ya fice ba dadewa Malam Arɗo suka shigo tare da zama kana suka yi Masa ta'aziyya ahankali Moddibo yace. “Ashe Ramadan lokaci yayi Allah ya masa rahma”. Cikin sanyi Lamiɗo yace. “Ameen Moddibo ya mukaji da taraddadin rashin Jameelu har yanzu shiru ko?”. Cikin sanyi Moddibo yayi ƙasa da kansa tare da matse yatsun hannunsa batare da yace Uffan ba sai kai da ya gyaɗa masa. Da-dai lokacin mai gadi ya sake shigowa tare da cewa. “Ranka ya daɗe ga Ɗan gidan Arɗo Ja'eh yazo yi maka ta'aziyya”. Kai Lamiɗo ya gyaɗa da fadin kace ya shigo”. Fita mai gadin yayi tare da sanar da baƙon. Da Sallama Bararojin Fulanin dajin yashiga falon Lamiɗo cikin shigarsu irin ta Fulani hannunsa riƙe da sanda kusa da ƙafar Lamiɗo ya zauna kana suka gaisa sannan ya musu ta'aziyya. Juyawa yayi ya kalli Malam, Arɗo, Moddibo, Alhj Musa Alhj Ibrahim ya gaishesu tare da yi musu ta'aziyya. Kallonsa Lamiɗo yayi kana yace. “Ori ya Baban naka?”. Cikin yanayin rashin wadatacciyar Hausa yace. “Ai bashi da lafiya ne shiyasa bai samu yazo ba, na wakilcesa munji labarin Ramadan ya rasu Allah ya masa rahma”. Baki ɗaya suka amsa da Ameen. Ahankali Lamiɗo ya juya tare da kallon Moddibo kana yace. “Moddibo da gaske wai har yanzu babu labarin Jameelu”. Ahankali Moddibo ya ɗago kansa dake ƙasa ya kalli Lamiɗo cikin rawan murya. “Eh har yanzu babu labarinsa, yanzu kam ma sun daina kira, sannan kuma wayarsa ma da ake kira ta daina shiga zuwa yanzu munsa hukuma a cikima sunyi iya bincikensu ba labari”. Malam Arɗo ne ya gyara zamansa tare da faɗin. “Ai wannan Zamani da Allah ya kawo mu sai dai Ubangiji ya rufa mana asiri amma an maida satan al'ummar kamar satan ƴaƴan awaki”. Ido Ori ya zuba masa tare da sakin Ajiyar zuciya. Malam Arɗo yace. “Kisan rai kuma ba adaukesa abakin komai ba, ran mutum ya dawo kamar ran kishiya, baki ɗaya duniyar nan ta canza ta burkice ta koma abin tsoro, in ba haka ba kamar Malam Jameelu asace sa bashi babu labarinsa”. Alhj Musa da Alhj Ibrahim kuwa kai suka jinjina da faɗin. “Sosai kuwa yanzu idan kana da dukiya hankalin ka ba akwance ba, haka zalika idan kana talaka ma baka da nutsuwa, sai dai Allah ya kawo mana ɗauki amma baki ɗaya jama'ar duniyar ta canza, yanzu ma idan muka fita daga nan zamuje wajen Alhj Bashir ɗin muyi masa jaje”. Malam Arɗo ya gyaɗa kai tare da cewa. “Muma yanzu daga can muka fito”. Jinjina kai Alhji Musa yayi da faɗin. “Allah sarki Jameelu yaro mai mutunci da karamci, ga sanin darajar manya Ubangiji ya bayyana shi”. Gyara zama Ori yayi tare da fuskantar Lamiɗo cikin rashin ingantaccen hausarsu yace. “Hmmm Lamiɗo wato ai wannan duniyar ta zama abin tsoro kwanan nan abinda na gani acikin dajin mu, saman dutsen Membilla aƙasan wata bishiya har zuwa yau hankalina bai gama dawowa jikinaba har zuwa yanzu wanda yasan ni da ya ganni ayanzu yasan ban gama dawowa cikin hayyacinaba”. Atare Moddibo da sauran jama'ar dake falon suka juya suka kallesa kusan a tare sukace. “Me ka gani?”. Girgiza kai yayi da faɗin. “Kai tashin hankalin fa ya tsananta, muda muke daji ai munfi ku ganin tashin hankali, ku ai kuna cikin gari ba abinda kuke gani sai dai in an ɗauke muku mutum kuke ganin tashin hankali”. Lokaci ɗaya zuciyar Moddibo ya tsinke da masifar ƙarfi yana bada sautin dib-dib-dib cikin sauri ya sanya tafin hannunsa na dama ya dafe saitin ƙahon zuciyarsa kana ya runtse Idanunsa yayin da gaba ɗaya ilahirin jikinsa ya hau kyarma wani zufa mai ɗumi ya keto Masa daga tsakiyar kansa cikin raunin murya yace. “Amma meyafaru meka gani bawan Allah!”. Girgiza kai Buba yayi da faɗin. “Abinfa ba daɗin gani, domin ya wuce tunanin mutum”. Ajiyar zuciya Malam Arɗo ya sauƙe tare da faɗin. “Toh Allah ya rufa mana asiri amma baki ɗaya zamani ya zama abin tsoro, to amma Ori mai kagani acikin dajin da har ya gigita ka haka, bayan ku Fulani daji kun saba ganin abubuwa!”. Cikin sauri Ori ya girgiza kai da faɗin. “Kai gane ganen da muka saba ba irin wannan bane! Duk abinda muke gani na yau da kullum lamuran iska ko halittun dajine”. Alhj Musa dake fuskantarsane yace. “To amma meka gani haka? Ya kamata idan kunga abu irin wannan na tsoro Ku riƙa faɗa acikin gari wurin jami'an tsaro”. Girgiza kai Ori yayi cikin sanyin murya yace. “Uhm muna tsoro ai”. Lamiɗo ne ya sauƙe Ajiyar zuciya da faɗin. “To amma meka gani?”. Gyara zama yayi tare da sauƙe ajiyar zuciya kana yace. “Abinda nagani abin tsoro ne, to amma dai banga amfanin ɓoye muku ba, yau tsawon kwana bakwai kenan ina kiwon shanu na akan Dutsen Membilla”. Duk ido suka zuba masa tare da maida nutsuwarsu kansa suna saurarensa. Gyara zama Ori yayi kana ya cigaba da cewa. “Ina nufar kan dutsen sabida ɗebo kanya, naji wani irin wari mai gigitarwa da fitar da hayyacin ɗan Adam Atake tsoro ya kamani na rasa wani irin wari ne wanan. Saboda ban taɓa jin wari makamancin wannan ba!”. Cikin sauri Lamiɗo ya kallesa da faɗin. “To wannan wani irin wari ne!?”. Ajiyar zuciya ya sauke da faɗin. “Hmmm Lamiɗo nima kaina na gigice. Saboda ban taɓa jin makamancin wari irin wannan ba a duniya!”. Alhj Ibrahim ya fesar da numfashi kana yace. “To amma me kagani awajen haka?”. Girgiza kai yayi da alamun damuwa atare dashi yace. “Ban taɓa ganin abinda ya tayar min da hankali ya kiɗimani ba irin wannan domin ina jin warin na haura na nufi wajen agindin wata Bishiyar kanya”. Cikin zaƙuwa da gajiyawa za tsinkewar zuciya Modibbo yace. “Uhmmm!!”. Shi kuwa Ori runtse Idanunsa cike da damuwa ya cigaba da cewa. “Ina haurawa kan dutsen. Naga gawa ɗaure a jikin bishiyar, da igiyoyi tako ina. Wanda da alamu abin ya kwana biyu domin tuni mutumin ya rasu gawace aɗaure, bisa ga duk kan alamu tunda ransa aka dauresa har ya rasu domin har ya kumbura yayi dam sai wani irin sheƙi fuskarsa duk sauran jinka keyi, fuskara ɗauke da murmushi duk da ya rasu, sai kuma alamun kwaranyar hawaye a kan kumatunsa gemunsa da sajensa sai sheƙi sukeyi tamkar wanda kullum ana shafa masa maine kai in ka ganshi kace balarabene wannan warin ne kaɗai ke nuni da gawane, domin a lokacin bai fasheba jikinsa fes”. Cikin sauri da wani irin azabebben tsinkewar zuciya Moddibo ya runtse Idanunsa tare da taune lips ɗinsa na ƙasa kana yace. “Innalillahi wa'inna ilahi rajiu'n Hasbunallahu wani'imal wakil”. Malam Arɗo kuwa cike da tsoro ya kalli Ori kana yace. “To amma kai Meyesa baka zo ka faɗa acikin gari ba!?”. Ajiyar zuciya ya sauƙe kana yace. “Tsoro nakeji domin Atake awajen na fara sheƙa amai da gudawa saboda warin dana shaka karshe ma agigice na koma gida, domin bana cikin nutsuwa ta kuma tunda na koma saida nayi kwana uku bani da lafiya ko kiwo sai ƙanina ne ya karba, kuma dole muka canza wajen kiwo saboda warin da wannan yankin keyi”. Cikin sauri da ɓacin rai Lamiɗo yace. “Haba Ori ya za ayi kuyi haka kuda kuke tare dani ai idan kunga makamancin abu irin wannan, sai ku kirani ku faɗa min idan yaso in tura ƴan sanda su duba ko menene ya za ayi kuyi shiru!?”. Cikin tsoro da cikekken gaskiya Ori ya sauƙe ajiyan zuciya tare da Girgiza kai kana yace. “Hmmm ire-iren waɗannan abubuwan gaba ɗaya mu Fulani ma zauna daji ake ɗaurawa alhakin sa, wanda bamusan komai ba banda Bautar Allah da kiwon dabbobin mu, amma baki ɗaya an ɗauki baƙin jini da tsana an ɗaura mana”. Kallonsa kawai suke zuciyarsu na tsinkewa. Shi kuwa a hankali ya cigaba da cewa. “Mutanen gari na cewa Fulani sune ƴan Kidnapping, to idan mun faɗi ire-iren waɗannan abubuwan sai azo ace mu muka aikata ayi ta kamamu, shiyasa mukeyin shiru, kuma nima Aruɗe na koma gida baki ɗaya bana cikin nutsuwa ta shiyasa”. Cike da damuwa Malam Arɗo yace. “Allah mai iko kai wannan zamani Allah ya rufa mana asiri”. Kallonsa ya mayar kan Moddibo da har zuwa lokacin jikinsa ke tsuma kana tun lokacin daya runtse Idanunsa har yanzu bai buɗe ba cikin sanyin murya Malam Arɗo yace. “Amma Moddibo ka shirya muje wajen mu duba gawan waye!”. Cikin sauri Moddibo ya buɗe Idanunsa dake rintse ya kallesa kana yace. “Nikam bazan jeba Malam Arɗo me kake nufi kana nufin J ɗina ne?”. Girgiza kai Malam Arɗo yayi tare da cewa. “Ba haka nake nufi ba bakaji bahaushe yace idan raƙumin ka ya ɓataba ko cikin ramin allura ka duba ba to muje mu duba mana”. Jinjina kai Lamiɗo yayi da faɗin. “Tabbas kam ya kamata aje aduba yanzu kuje ku faɗawa Mahaifinsa Ni kuma zan kira hukumar ƴan sanda sai muje dasu”. Girgiza kai Moddibo yayi tare da fesar da numfashi mai zafi kana cikin rawan murya yace. “Nifa bazan jeba dan nasan in Sha Allah ba J ɗina bane, bakuji yace muku gawa bane kuma tuntuni ya mutu har ya kumbura ni kuma J ɗina bai mutuba inaji Ajikina in Sha Allah yana raye”. Dafa kafaɗar sa Malam Arɗo yayi tare da cewa. “Moddibo kada kiɗima yasa ka furta kalmar alamar sanin gaibu”. Cikin sauri Moddibo ya Girgiza kai kana muryarsa na rawa yace. “Astagafirullah³ amma dai inaji Ajikina kamar J ɗina yana raye”. Cikin sanyin murya Malam Arɗo yace. “Eh duk da haka dai muje”. Girgiza kai yayi tare da cewa. “Nifa bazan jeba”. Cikin lallashi Lamiɗo yace. “A'a Moddibo ka daure dai kuje Allah yasa ba shiɗin bane amma dai aje aduba ɗin”. Kai Buba ya gyaɗa kana yace. “Eh suje su duba kuma alokacin ma na samu an ajiye wayoyi agabansa da kuma goran ruwa fuskarsa ma bata wani kumbura ba dan kyanshi bai ɓaceba”. Atsorace Moddibo ya kallesa zuciyarsa na bugawa da masifar ƙarfi yace. “Harda waya kuma shikenan bari Muje mu gani ɗin?”. Ya faɗa tare da miƙewa suka fita kai tsaye gidan Abba suka nufa kana malam Arɗo ya masa bayani. Kallon Abba Moddibo yayi cikin raunin murya yace. “Abba ni dai inaji Ajikina in Sha Allah ba J ɗinmu bane, amma dai tunda sunce muje to muje ɗin”. Cikin rarrashi Malam Arɗo yace. “Alhj kayi haƙuri muje mu gani”. Cikin sanyi da rauni kana da tsinkewar zuciya Abba ya gyaɗa kai dai-dai lokacin da folisawan suka iso tare da Lamiɗo. Fita sukayi cikin shirin tafiya Abba, Lamiɗo malam Arɗo da Moddibo suka shiga mota ɗaya Ori kuma ya shiga motar Ƴan sanda suka tafi. Suna isa dajin bayan sunyi Parking din Motar daga can nesa, suka fara haurawa saman dutsen. Da sauri suka fara kallon juna sabida jin wani irin ni'imtaccen ƙamshi mai sanyin shaƙa, babu wari kamar yanda ya faɗa musu yasa Moddibo juyawa ya kalli Ori kana cikin sanyi yace. “Ya gaba ɗaya babu warin da kace sai ma wani irin amintaccen ƙamshi”. Kallonsa Ori yayi da faɗin. “Toh yaufa kusan kwana takwas kenan da labarin dana baku ai dole wari ya baje dan zuwa yanzu Nasan gawar ya fashe bare kuma ruwan sama da ake ai dole zai za gonye sai dai kuma nima nayi mamakin wannan ƙamshi!”. Cikin sanyi Malam Arɗo yace. “Allah mai iko wannan wani irin ni'imtaccen ƙamshi ne a tsakiyar daji”. Abba kuwa kasa furta komai yayi sai zuciyarsa dake bugawa da masifar ƙarfi yana jin wani irin masifaffen tsinkewar zuciya haka zalika Moddibo suna masu shaƙar ƙamshi. Lamiɗo da polices din kuma sai lumshe idanu suke sabida daɗin ƙamshin da Ubangijin talikai ya wadata wurin dashi. Yayinda suna kara haurawa suna ƙara jin ƙamshin. Cikin tsanananin fargaba da tsinkewar zuciya suka cigaba da haurawa wajen suna gama haurawa Ori yayi saurin cewa. “Yawwa ga can bishiyar”. Da sauri Moddibo ya ɗaga Idanunsa tare da kallon jikin Bishiyar ganin gawa ɗaure ajikin Bishiya yayi har ya zagwanye idanunsa sun rarake sai ramuka kaɗai sai kuma maiƙo dake zube aƙasa da wani irin sassayan ƙamshin dake tashi a wurin. Cikin tsanananin tsinkewar zuciya ya sauƙe idanunsa akasa dai-dai kan ƙafar gawar dake maƙale da takalmin cikin sauri ya runtse Idanunsa tare da dafe ƙahon zuciyarsa dake bugawa da masifar ƙarfi. Abba kuwa da sauri ya ƙarasa jikin Bishiyar dai-dai Inda goran faron ke ajiye Idanunsa suka sauƙa akan wayoyin dake wajen hannunsa na rawa ya ɗago wayar tare da jujjuyawa. Cikin tsanananin tashin hankali da ruɗu yace. “Innalillahi wa'inna ilahi rajiu'n!”. Juyawa yayi tare da kallon Moddibo cikin raunin murya yace. “Aliyu wayoyin Jameelu na neeeee”. Cikin sauri Moddibo ya juya tare da dafe saitin ƙohon zuciyarsa cikin raunin murya mai cike da tsantsar tashin hankali yace. “Abba wayar J kuma”. Kai Abba ya gyaɗa yayin da wasu irin hawaye masu masifar zafi ke koro juna subabin kuncinsa murya na rawa yace. “Eh”, Ahankali Moddibo ya juya ta gefen da gawar ke daure tare da tsaida idanunsa akan hannun gawar na dama da har ya bushe idanunsa ya zubawa zoben dake hannu gawar. Cikin tsanananin kaɗuwa da wani masifaffen tsinkewar zuciya mai cike da ɗimuwa da tashin hankali Moddibo yace. “Innalillahi wa'inna ilahi rajiu'n Abba kalli zobunnan hannunsa zobunnan hannun J ɗina ne da agogon”. Ya ida maganar tare da yanke jiki ya faɗi babu numfashi atare dashi....! Wannan littafin dai na kuɗi ne. By *GARKUWAR MARUBUTA* [30/07, 1:42 PM] Halimatu A/rahman Sadeeya: Spndeɗɗ. Baya Moddibo ya koma. Suuuuuu ya faɗi a sume, cikin sauri Lamiɗo ya tarosa, ya faɗa jikinsa cike da tashin hankali Lamiɗo yace. “Innalillahi ya suma fa Subhanallah!”. Cikin sauri Malam Arɗo ya ƙara sa kusa da Lamiɗo idanunsa akan Moddibo ya shiga kiran sunan sa yana faɗin. “Moddibo!, Moddibo!!, Moddibo!!!”. Ina tuni Moddibo ya sume babu alamar numfashi atare dashi. Abba kuwa kansa ya ɗaga tare da kallon fuskar skeleton M Jameel kana ya maida Idanunsa ƙasa kan takalmin dake sanye aƙafarsa ahankali ya leƙa bayan idanunsa suka sauƙa akan guntun rigarsa da bai gama sauƙa daga jikin skeleton ba jinjina kansa yayi cikin wata dakakkiyar murya ya juya ya kalli Moddibo dake sume kai ya girgiza tare da sakin murmushin da yafi kuka ciwo murmushi da yafi ihu zafi, murmushin da yafi ciwo, Ciwo murmushin da yafi raɗaɗi zafi, ya saki kana ya juya ya kalli sauran mutanen dake tsaye sai ya kuma kalli fuskar skeleton tare da maida kallonsa kan yatsun hannunsa. Cikin wata dakakkiyar murya me ɗauke da tarin raɗaɗi da ƙuna yace. “Uhmmm Jameelu na ne”. Kallonsa ya mayar kan Moddibo da har zuwa lokacin yake. Rungume a jikin Lamiɗo taune lips ɗinsa yayi tare da cewa. “Kai kam Aliyu kahuta, inama ace nima zan sume ko kuma in mace ma gaba ɗaya da hakan yafi min sauƙi”. Cikin sauri ɗaya police ɗin ya juya tare da isa gefen Abba ya riƙe sa cike da alhini da tarin tausayawa yace. “Alhj Bashir kayi addu'a kaji”. Kai Abba ya gyaɗa cikin wata dakakkiyar murya yace. _“Innalillahi wa'inna Ilahi rajiu'n lahaula wala ƙuwwata Illah billahil aliyul Azhim Hasbunallahu wani'imal wakil Allahumma Ajirni fii musibati wa'ahlifli khairan minha La'ilaha Illah anta subhanaka Inni kuntu Minal Zhalimin”_ sune Adduo'in da yake iya maimaitawa afili da kuma ransa. Ori dake tsaye ciki ruɗu da tausayawa yayi saurin ƙarasawa gaban skeleton gawar M Jameel ya ɗauko goran ruwan kana ya dawo tare da miƙawa Lamiɗo yana mai cewa. “Lamiɗo gashi ayayyafa masa”. Karɓa Lamiɗo yayi kana ya buɗe tare da yayyafawa Moddibo dake kwance jikinsa amma ko kaɗan Moddibo bai motsa ba. Kallon Buba Lamiɗo yayi kana yace. “Ori taimaka min mu saka shi cikin Mota”. Kai Buba ya gyaɗa. Ɗaya daga cikin Folisawan ne yace. “Ranka shi daɗe bari mu saka shi”. Ya faɗa tare da kallon ɗan gidansa da Ido ya masa alamar yazo su kama Moddibo ƙarasawa yayi sannan suka ɗauki Moddibo suka sauƙa kasan dutsen, tare da sanya shi abayan Motar Malam Arɗo. Folisawan kuwa ƙara sawa sukayi suka shiga ɗaukar hoton gawar skeleton M Jameel. Bayan sun gama ɗauka tare yan dube-dubensu, da Babbansu da sauran suka saka handglove suka ƙarasa gaban gawar da niyyar sunjanye gawar Babbansun najan Igiyar da aka ɗauɗaureshi ƙasusuwan suka kakkarye tare da zubewa a ƙasa babu ta yanda zasu iya daukarsa Babban su ya umarci Coustable yaje ya ɗauko musu kwali abayan mota kana suka tattara gawar suka zuba acikin kwalin kana suka kwashe takalmansa da wayoyinsa suka saka awata leda. Abba kuwa cikin wani irin yanayi ya nufi cikin jejin yana tafiya ba tare da shi kansa yasan inda ya nufaba. Cikin sauri Lamiɗo ya nufesa tare da riƙe hannunsa cike da tausayawa yace. “Alhj banan zamu bi ba can baya ne, hanyar kazo innu na maka hanyar da zamu bi”. Kai Abba ya gyaɗa tare da bin bayan Lamiɗo baki ɗaya baya cikin nutsuwarsa ya kasa gane shin mafarki yake ko kuma azahirance komai ke faruwa. Bayan sun isa Lamiɗo da kansa ya buɗe masa mota yashiga sannan shima yashiga. Folisawan kuwa kwalin da gawar M Jameel ke ciki suka ɗauka tare da sawa abayan motarsu suka tafi gida. Abba kuwa kallon hanya kawai yake baki ɗaya baya cikin hayyacinsa ganin yanayin da yake ciki ne yasa Malam Arɗo ya fara yi masa Adduo'i yana tofa masa kana yana faɗa afili. Ahankali Abba ya fara sakin Ajiyar zuciya kana yashiga maimaita Adduo'in sannu Ahankali ya fara jin hankalinsa ya fara dawowa jikinsa. Motar da Moddibo ke ciki Ori da police ɗaya ne aciki direct Asibiti suka nufa dashi. Yayin da Motar dasu Abba da kuma gawar M Jameel ke ciki kai tsaye gida suka wuce, suna isa kai tsaye falonsa suka wuce police ɗin ne ya ɗauko kwalin Gawar M Jameel ya shigo dashi kana ya ajiye agabansu. Hajiya Turai dake sashenta tana jin tsayuwar motoci ta fito zuwa falon Abba. Ganin Abba zaune tare dasu Lamiɗo yasa ta nufi gefen Abba cikin yanayin damuwa tace. “Alhj lafiya ya ake ciki Gawar waye kuka samu?”. Ahankali ya ɗago Idanunsa da suka kaɗa sukayi jawur ya kalleta kana yayi ƙasa da kansa cikin raunin murya yace. “Gawar Jameelu na ne!”. Arazane Hajiya Turai ta kallesa zuciyarta na bugawa da masifar ƙarfi Idanunta akansa tace. “Gawar Jameelu kuma!?”. Kai ya gyaɗa mata Cikin tsananin tashin hankali da ruɗu ta fashe da kuka me tsuma zuciya tana furta. “Innalillahi wa'inna ilahi rajiu'n ina gawar yake?”. Da hannu ya nuna mata kwalin dake gabansa. Da kallo tabi kwalin cikin sauri ta sake Kallonsa Idanunta cike da ruwan hawaye tace. “Gawar Jameelu ne acikin kwali haka?”. Kai ya gyaɗa batare daya ɗago kaiba yace. “Shine”. Wani sabon kuka ta fashe dashi tana Girgiza kai Kukanta ne ya fito da Hajiya Karima itama ganin abinda ke faruwa yasa ta fashe da kuka. Acan Asibiti kuwa ana kai Moddibo likitoci suka shiga bashi temakon Gaggawa saidai koda wasa bai farfaɗo ba ganin haka yasa suka dauƙo wani na'ura mai kama da Iron akafara danna masa aƙirji. Amman ina babu alamun zai motsa, sosai likitocin suka dugufa wurin ganin sun cetoshi, a karo na biyu suka kuma danna mishi a ƙirjunshi, amman ina, Dr Lukman ne ya karɓi aikin tare da goggoga jikin na'urar ya manna masa a kirjinsa da ƙarfi. Cikin ikon Allah yaja wani dogon numfashin sake dannawa yayi da karfi wani irin maraitaccen numfashi ya sake ja amma still bai farfaɗo ba sake dannawa sukayi akaro na biyar ne yaja wani dogon numfashi tare da buɗe idanunsa kana yace. “Jyyyyyyy”. Malam Arɗo da bai daɗe da dawowa daga gidan Abba bane, yayi saurin riƙe hannunsa tare da cewa. “Moddibo kayi addu'a”. Duk da cewa baya Cikin nutsuwarsa hakan bai hanashi maimaita duk wata addu'a da tazo bakinsa ba ahankali ya ɗago kansa tare da kallon Malam Arɗo yace. “Malam J ɗina nefa!”. Jinjina kai Malam Arɗo yayi cike da tausayawa yace. “Eh shine Moddibo Allah ya karɓi Jameelu muyi masa addu'a Allah ya karɓi shahadarsa”. Girgiza kai Moddibo yayi tare da cije lips ɗin sa duka biyu, kana ya runtse Idanunsa cikin wani irin yanayi mai wuya yace. “Malam Arɗo mutuwar azaba suka masafa, ɗaure sa sukayi suka ajiye masa goran ruwan agabansa ta yanda yana ji yana gani bashi da damar sha sun barshi da azabar ƙishi”. Kallonsa Malam Arɗo keyi cike da tausayawa yana ganin yanda zuciyarsa ke bugawa da ƙarfi. Cikin wata raunan'niyar murya Moddibo ya cigaba da cewa. “Malam ɗaure sa sukayi suka ajiye masa wayoyinsa agabansa ta yanda yana kallon muna kiransa bashi da damar ɗauka bare yace mukawo masa ɗauki”. Sai kuma ya rintse idanunsa da masifan ƙarfi zuciyarsa na cigaba da buguwa da masifaffen ƙarfi kana yace. “Ɗaure sa sukayi ta yanda yana ganin ga hanyar tsira sai dai bashi da damar kiran wani ya kawo masa ɗauki ɗaure sa fa sukayi ta yanda yana ganin kiran mu amma bashi da damar ɗauka”. Jujjuya kansa ya farayi kamar zautacce hawaye na bin gefe da gefen idanunsa har suna shiga kunnensa cikin Muryan kuka yace. “Ɗauresa fa sukayi ta yanda yana ganin kiran Abbansa bashi da damar ɗauka,Mutuwar azaba da raɗaɗi suka masa da ƙishi fa suka kasheshi”. Kasa ƙarasa maganar yayi kawai ya fashe da matsanancin kuka mai tafiya da numfashi Atake numfashinsa ya ɗauke ya sake sumewa!. Cikin sauri Malam Arɗo ya miƙe tare da kiran likitoci kana ya sanar dasu ya sake suma taruwa likitocin sukayi akansa kana suka shiga bashi temakon Gaggawa da kyar da temakon Allah suka samu ya farfaɗo ganin ya farfaɗo yasa Dr ya masa Alluran bacci Atake baccin wahala ya ɗauke sa. Ajiyar zuciya Malam Arɗo ya sauƙe tare da miƙewa ya fita kana yayi dearling number Lamiɗo yana ɗauka yace. “Ranka shi daɗe yaron nan fa gashi agigice yake baki ɗaya da zaran ya farfaɗo sunan Marigayi Jameelu yake kira, yana kiran sunan kuma zai sake suma!”. Acan gidan Abba kuwa zaune yake afalonsa hannunsa riƙe da waya tunda suka dawo yake zaune awajen ya kasa koda motsawa se kwalin Gawar Jameelu daya zubawa Ido yana jujjuya wayar hannunsa ajiyar zuciya ya sauƙe tare da kiran number Ummi Yana Jin tayi picking ya fesar da numfashi kana yace. “Fatima”. Cike da mamaki Ummi tace. “Abban Jameel”. Jin muryansa. Cikin raunin murya ya sake cewa. “Fatima”. Anutse Ummi ta amsa da. “Na'am”. Runtse Idanunsa yayi kana yasake cewa. “Fatima”. Cikin dakiya Ummi da taji zuciyarta ya tsinke da Masifar ƙarfi tace. “Na'am Abban Jameel ka faɗa min me yasamu Jameelu na sun kira ne ko kuma yaya!?”. Cikin rauni yace. “Hmmm”. ya faɗa tare da katse kiran kana ya fito da Number Malam Ahmad. Malam Ahmad na ɗagawa Abba yace. “Malam kazo da Fatima da yaranta!?”. Cikin tsinkewar zuciya Malam Ahmad dake Bedroom ɗinsa ya miƙe tare da cewa. “Meya faru Alhj Bashir ka faɗa min”. Girgiza kai Abba yayi tare da taune lips ɗinsa kana yace. “Ga gawar Jameelu na agabana”. Cikin tsanananin tashin hankali Malam Ahmad ya dafe bango tare da faɗin. “Innalillahi wa'inna ilahi rajiu'n Allahumma Ajirni fii musibati wa'ahlifli khairan minha”. Katse kiran Abba yayi cikin sauri ya fito falon tsaye ya samu Ummi riƙe da waya a hannunta cikin ƙoƙarin ɓoye tashin hankalin sa yace. “Fatima Lafiya!?”. Ahankali Ummi ta juya ta kallesa tare da cewa. “Yan zun nan Abban Jameel ya kirani, to kuma ya yanke gashi kuma ina ta sake kira naji line Busy”. Da ƙyar ya haɗiye wani abu mai masifar ɗaci kana cikin ƙoƙarin ɓoye damuwarsa yace. “Toh kada ki damu kizo muje muji meke faruwa”. Kai ta gyaɗa tare da cewa. “Toh”. Sannan ta nufi hanyar fita. Kallon Bashir da Asma'u dake tsaye yayi kana yace. “Kuma kuzo mu tafi”. Kai suka gyaɗa kana suka bi bayansa suka fita. Suna isa falon suka samu Hajiya Turai da Hajiya Karima da ƴaƴan Hajiya Karima na kuka cikin sauri Ummi ta ƙara sa shiga falon tare da tsayawa agaban Abba kana tace. “Abban Jameel meye faru?”. Ahankali ya ɗago ido ya kalleta, sai alokacin yaji kuka ya kufce masa ganin Ummi agabansa baki ɗaya ta gigice jikinta na rawa. Cikin rawan murya tace. “Abban Jameel meyafaru!?”. Kasa cewa komai Abba yayi sai kuka da yake tamkar ƙaramin yaro. Da sauri Ummi ta juya tare da kallon yanda su Hajiya Turai ke kuka cikin rawan murya da yanayin tashin hankali tace. “Ku faɗa min mana meke faruwa!?”. Tayi tambayar baki ɗaya ilahirin jikinta na rawa. Asma'u da Bashir dake tsaye Atare suka fashe da matsanancin kuka ganin yanda ƙannen M Jameel ke kuka. Ahankali Malam Ahmad ya matso kusa da Ummi tare da cewa. “Fatima ki zauna”. Girgiza kai tayi kana tace. “Ni bazan zauna ba kafaɗa min abinda ke faruwa”. Cikin sanyin murya Lamiɗo yace. “Maman Jameel kiyi haƙuri ki zauna”. Kallon sa tayi tare da cewa. “In zauna?”. Kai ya gyaɗa mata kana yace. “Eh”. Cike da tausayawa Malam Ahmad ya janyo hannunta tare da zaunar da ita. Abba kuwa kallonta yayi cikin tsanananin fargaba da tashin hankali yace. “Fatima”. Cikin rawan murya da raunin zuciya tace. “Na'am Alhj Bashir”. Cikin sauri Abba ya kalleta wannan shine karo na farko arayuwar sa da yaji ta kira sunan shi kai tsaye. Jinjina kai tayi Idanunta tsaye akansa tace. “Eh Alhj Bashir ka faɗa min menene? kafaɗa meke faruwa”. Rintse idanunsa yayi yana jin kansa na sarawa Araunane yace. “Fatima Jameelun mu”. Kai ta gyaɗa kana tace. “Eh nasani akan Jameelu ne to Menene ya faru?”. Kasa cewa komai Abba yayi kawai sai ya fashe da matsanancin kuka yayin da hawaye ke bin kuncinsa Shar-shar-shar. Cikin raunin murya yace. “Fatima ga Gawar Jameelun mu”. Atake maganar ya daki dodon kunnenta kana ya ratsa ƙwaƙwalwar ta zuwa zuciyarta saurin kallon Abba tayi tare da sakin Murmushi kana ta juya tare da kallon su Hajiya Karima dake kuka cikin wata dakakkiyar murya mai cike da ƙuna tace. “Toh kukan me kukeyi!?, Juyawa tayi tare da kallon Abban M Jameel kana tace. “Har kaima kuka kakeyi!?Haba Alhj Bashir Addu'a ya kamata ka masa amma ba kuka ba!, Su mata suyi kuka kaina kayi Yanzu ina yake?”. Cikin sheshsheƙan Kuka Abba ya nuna mata kwalin da ya tsarsa kana yace. “Gashi can”. Saurin Kallon wajen tayi Zuciyarta na bugawa da masifar ƙarfi still Muryanta adake da wani irin bushewa da hurawar zuciya tace. “Gawar ne kuma acikin kwali”. Cikin wata raunan'niyar murya ya Girgiza kai kana yace. “Kiyi haƙuri kiyi ta maimaita Addu'a”. Ajiyar zuciya ta sauƙe tare da rintse Idanunta kana tace. “Innalillahi wa'inna ilahi rajiu'n Hasbunallahu wani'imal wakin La'ilaha Illah anta subhanaka inni kuntu Minal Zhalimin Allahumma Ajirni fii musibati wa'ahlifli khairan minha³”. Ahankali ta gyara zamanta tare da naɗe ƙafafunta tare da sakin murmushi kana ta fuskanci gabas yayin da Idanunta suka kaɗa sukayi jawur jikinta na wani irin tsuma na tsananin tashin hankali cikin raunin murya tace. “Ya Allah kaine ka bani Jameelu, kai kasa ya zamemini Garkuwa, ya Allah kajiƙan sa da rahma, ya Allah kasa ya huta Alfarman Annabi da Alkur'ani, Allah kayi mana SAKAYYAH akan dukkan waɗanda suka cutar damu ya Allah kayi mana SAKAYYAH”. Kusan a haɗe baki daya mutanen falon suka amsa da Ameen. Wani irin kuka mai tsuma zuciya ne ya kufcewa Asma'u da Bashir musamman Asma'u numfashinta har fisga yake baki ɗaya Falon kaurewa yayi da koke cikin rawan murya Ummi tace. “Ina gawar yanzu Jameelu na ne haka acikin kwali?”. Jinjina mata kai Abba yayi tare da cewa. “Eh shine”. Still Muryanta adake tace. “Wani irin mutuwa yayi da har gawarsa zata ƙankace ya zauma acikin kwali”. Asp dake tsaye ya kalli Ummi cike da tausayawa yace. “Hajiya kiyi haƙuri ya riga daya bushe, shiyasa ana taɓa shi ya kakkarye!”. Ahankali ta juya ta kalli Asp kana tace. “Toh ya akayi kuka tabbatar Jameelu na ne?”. Cike da tausayawa Asp ya ƙara sa gaban Kwalin kana ya buɗe mata ahankali Ummi ta tsirawa jerarrun gabɓan gawar dake cikin kwalin ido ahankali ta sauƙe Idanunta akan zara-zaran yatsun, hannunsa da suka bushe kana ta tsirawa zoben hannunsa ido. Cikin wani irin yanayi na ƙunan zuciya da sadaukarwa tace. “Hmmm!”. Ahankali Asp ya sake nuna mata takalmin M Jameel dake cikin leda da kuma wayoyinsa cikin sanyin murya yace. “Ga takalmansa da kuma wayoyinsa duk agabansa muka samu sun ajiye masa da goran ruwa. Ajiyar zuciya ta sauƙe tare da fesar da numfashi kana tace. “Tabbas Jameelu na ne”. Ahankali ta matsa jikin kwalin sosai tare da sanya tafin hannunta ta rufe kana ta sunkuyar da kanta akan kwalin cikin Muryan ta daya fara karaya tace. “Babana bazan yi maka kuka ba, sannan baza zubar maka da hawaye ba, kana bazan yi maka Ihu da kururuwa ba, amma zan ƙarashe baki ɗaya sauran rayuwata ina maka addu'a, zan ƙare rayuwata da ƙunan rashinka zan ƙare rayuwata babban giɓin rashinka”. Wani irin tausayinta ya ratsa baki ɗaya jama'ar dake falon ahankali Malam Ahmad da Lamiɗo suka sanya hannu tare da share hawayen da suka saƙƙo musu. Cike da rauni Ummi ta cigaba da cewa. “Babana zan ƙare baki ɗaya sauran rayuwata ina maka addu'ar Ubangiji ya karbi shahadarka Allah ya maka SAKAYYAH tun daga nan duniya akan wa anda suka zalince ka har zuwa ranar tashin Alkiyama. Allah Ubangiji yajiƙan ka da rahma Allah ya gafarta maka yasa kahuta”. Cikin sauri Hajiya Turai ta ƙarasa kusa da ita tare da Rungumeta ajikinta kana cikin Muryan kuka tace. “Kiyi haƙuri Hajiya Fatima kiyi shiru”. Kallonta Ummi tayi still Muryanta adake tace. “Idan banyi haƙuri ba Hajiya Turai ya zanyi. Ubangijin daya ɗauke Jameelu shi yabani shi kuma shi ya ɗauke sa kana ya fini sanin wanene Jameelu agareni, sannan ya fini sanin Jameelu Allah ya masa rahma”. Ta ida maganar tare da janye Jikinta daga na Hajiya Turai tare da juyawa ta kalli Abba kana tace. “Ina Moddibo!?”. Tana gama fadar haka tayi baya tare da sumewa. Cikin sauri Hajiya Karima ta mike tare da ɗauko ruwa ta yayyafa mata dogon numfashi Ummi taja tare da buɗe Idanunta kana tace. “Ina Moddibo yake?”. Cike da tausayawa Abba yace. “Moddibo yana asibiti asume tunda abin ya faru daya farfaɗo idan ya kira sunan Jameel zai sake sumewa, yanzu ne da aka samu ya farfaɗo aka masa Alluran bacci”. Araunane tace. “Ku kaini inga Moddibo sannan kada aje abinne Jameelu abari sai Moddibo ya farfaɗo yaga J ɗinsa na ƙarshe ya tabbatar cewa J dinsa tafi ya barsa bari na har abada, idan yaga haka zai dangana ya sawa ransa haƙuri amma yanzu dan Allah ku kaini wajen Moddibo”. Abba ne yace. “Yanzu zaki tafi can?”. Kai ta gyaɗa tare da cewa. “Eh ku kaini wajensa”. Ahankali Malam Ahmad ya miƙe tare da riƙe hannunta suka tafi. Asma'u da Bashir kuwa kuka suka sake fashewa dashi har muryarsu baya fita saboda tsananin tashin hankali. Rintse Idanu Abba yayi cike da tausayawa ya kallesu kana yace. “Ku daina kukan nan kuyi masa addu'a babu abinda Jameelu ke buƙata awajenmu yanzu kamar addu'a. Acan asibiti kuwa Ummi da Malam Ahmad na isa a reception suka samu Malam Arɗo tsaye ganinsu yasa ya ƙara sa kusa dasu kana yace. “Maman Jameelu kiyi haƙuri. Ubangiji Allah ya jikansa da rahma Allah ya gafarta masa Ubangiji ya amshi shahadarsa”. Cikin sanyin murya tace. “Ameen Malam Arɗo ina Moddibo?”. Ahankali ya gyara tsayuwar sa kana yace. “Gashi can yana ciki”.Ya faɗa tare da shiga gaba Ummi da Malam Ahmad na biye dashi. Suna shiga ɗakin Ummi ta zubawa Moddibo idanu dake kwance plat Fuskarsa tayi fayau duk da bacci yake amma tashin hankali da fargaba ne kwance asaman fuskarsa. Ahankali ta riƙe hannunsa acikin nata kana tace. “Moddibo munyi rashi, rashin da baza mu maimaita gurbinsa ba, munyi rashi rashin da har abada ba zamu mance shiba, munyi rashi rashin da saidai namu mutuwar ne zai mantar mana dashi”. Moddibo kuwa duk da Alluran baccin dake jikinsa hakan bai hana shi jiyo sautin muryan Ummi ba. So yake ya farka domin kunnuwansa na sauraronta haka zalika yana iya motsa gaɓɓansa sai dai koda ya buɗe idanunsa baya ganin komai cikin wani irin yanayi ya damƙe hannun Ummi acikin nasa, yayinda zuciyarsa ke cigaba da bugawa da masifar ƙarfi. Kallon Malam Ahmad Malam Arɗo yayi kana yace. “Toh tunda kunzo bari na wuce na faɗawa Kakarsa halin da ake ciki”. Jinjina kai Malam Ahmad yayi tare da cewa. “Ya kamata kam aje afaɗa mata sannan itama ataho da ita”. Kai Malam Arɗo ya gyaɗa kana ya juya ya fita kai tsaye gidan su Moddibo ya nufa yana isa yayi Parking ɗin motarsa kana ya shiga gate din farko ya daga sautin muryarsa tare da yin sallama. Cikin sauri Innayi ta fito ganinsa yasa ta saki Ajiyar zuciya tare da cewa. “Alhamdulillah dama yanzu nake tunanin in kira ka dan. Moddibo tun safe daya fita bai dawo ba, duk da cewa dama yanzu bai cika dawowa da wuri ba”. Ajiyar zuciya Malam Arɗo ya sauƙe kana yace. “Ki zo mutafi”. Saurin Kallonsa tayi kana tace. “Ina zamuje”. Cikin sanyin Murya Malam Arɗo yace. “Wajen Moddibo zamuje yana asibiti”. Da sauri ta dafe ƙirjinta sai kuma ta juya ta nufi cikin gida hijabinta ta ɗauko ta sanya kana ta rurrufe kofofin gidan kafin ta fita. Bayan sun fara tafiya acikin motar Malam Arɗo ya kalli Innayi kana yace. “An samo gawar Jameelu fa!”. Cikin tsanananin ruɗu da tashin hankali ta dafe ƙirjinta tare da faɗin. “Gawar Jameelu kuma?”. Kai Malam Arɗo ya gyaɗa kana yace. “Eh gawar Jameelu aka samu sun kashe sa”. Atake hawaye suka shiga zubowa Innayi cikin tashin hankali da jimami ta saki sassayan kuka tare da addu'o'i. A dai daren wannan ranar haka kowa ya kwana cikin ƙunci da raɗaɗi azuciya. Asp da tawagarsa sun koma gida bayan sun gama dukkan abinda ya dace na bincikensu, haka zalika Lamiɗo ma ya koma gida Abba kuwa kwana yayi da gawar Jameelun sa agabansa batare daya rintsa ba. Asma'u kuwa Hajiya Turai ta jata zuwa ɗakinta Anan ta kwana duk da cewa ba tayi bacci ba. Bashir kuwa aɗakin ƙannen M Jameel ya kwana tare dasu Aɓangaren Moddibo kuwa haka ya kwana cikin wani irin yanayi shi ba bacci ba kuma kuma shiba Ido biyu ba ba kuma a sumeba. Ana kiran Assalatun Farko acikin kunnen Moddibo sannu Ahankali ya fara bude idanunsa da yaji sunyi masifar nauyi har ya sauƙesu akan Ummi dake riƙe da hannunsa Idanunta abushe alamar ko rintsawa ba tayi ba bare kuma bacci. Cikin wata murya mai cike da karaya da kuma rauni yace. “Ummi”. Kallonsa Ummi tayi tare da faɗin. “Na'am Aliyu”. Girgiza kai yayi yayinda zuciyarsa ke cigaba da bugawa da masifar ƙarfi yace. “Ummi J ɗina”. Cike da tausayawa ta rintse Idanunta kana tace. “Aliyu kayi haƙuri”. Cije Lips ɗinsa yayi tare da damƙe hannunta acikin nasa kana yace. “Ummi J ɗina”. Jinjina kai tayi tare da sauƙe ajiyar zuciya tace. “Kayi haƙuri kaje kayi sallah duk abinda kake ji Aranka kana so ka faɗa min ka faɗawa Ubangiji”. Cikin sauri Malam Ahmad dake tsaye ya ƙara so bakin gadon tare da riƙe hannun Moddibo cikin sanyin murya yace. “Kayi haƙuri kaje kayi alwala”. Kallon Malam Ahmad Ummi tayi kana tace. “Toh ni yanzu zan tafi gida”. Girgiza kai Malam Ahmad yayi tare da cewa. “A'a ki bari mu tafi gidan Alhj Bashir yanzu”. Girgiza kai tayi kana tace. “A'a mu tafi gidanmu dai”. Girgiza mata kai yayi kana yace. “A'a gidan Alhj Bashir zamu je acan fa za ayi jana'izar mu tafi can ɗin!”. Shiru kawai Ummi tayi ahankali. Moddibo da har yanzu hannunsa ke cikin nata yace. “A'a Ummi dan Allah muje gidan Abba”. Kai ta gyaɗa masa cikin sanyi tace. “Toh shikenan”. Batare da an sallamesu ba suka fita Moddibo da Malam Ahmad suka shiga gaba Ummi tashiga baya Anutse Malam Ahmad yayiwa motar key kana yaja suka bar Asibitin kai tsaye gidan Abba suka nufa suna isa Malam Ahmad ya danna hong ta cikin ƙaramin ɓulin. Mai gadi ya leƙa jin ana ta danna hong ganin motar da tazo jiya da safe ne yasa ya koma cikin gida tare da sanarwar Abba yaga motar da jiya tazo yauma ta dawo. Kai Abba ya gyaɗa kana yace. “Eh kaje ka buɗe musu Maman Jameel ne yanzu aka sallame su daga asibiti kaje ka buɗe musu”. Kai ya gyaɗa sannan ya buɗe musu gate din suka shiga bayan Malam Ahmad yayi Parking suka fito kai tsaye falon Abba suka shiga. Zaune suka samesa shi kaɗai a falon hannunsa riƙe da Carbi ya tsirawa kwalin Gawar Jameel Ido. Ahankali Ummi ta ƙarasa tare da zama agefen kwalin shima Moddibo zama yayi agefen kwalin Malam Ahmad ma ya zauna agefen kwalin sai ya zamana sun saka kwalin Atsakiyar su. Moddibo kuwa kallon kwalin yayi kana ya kalli Ummi cikin raunin murya yace. “Ummi yanzu J ɗinane aciki?. Ummi da gaske J ɗina ne ya rasu!?”. Kai Ummi ta jinjina kana tace. “Da gaskene Moddibo, tabbas Jameelu ne yarasu Jameelu ya tafi yabar mu bari na har abada, ba zamu sake ganinsa ko jin sautin muryarsa ba sai dai ahoto”. Girgiza kai Moddibo yayi tare da ɗaura kansa akan kwalin ya fashe da wani irin kuka me tsuma zuciya cikin sheshsheƙan Kuka yace. “Yanzu shikenan J ɗina mun rabu har abada bayan yana burin yin Aure ya zauna gida ɗaya da Ummi da ƙannensa yanzu shikenan wannan burin ya tafi”. Ya sake Rungume Kwalin tare da cewa. “Yanzu shikenan J ya tafi ya barni shin dawa zan rayu duk wani farin ciki ne da walwala na J ɗina ne shin waye zai fahimcini a duniya? J ɗina ne kaɗai yake iya fuskarta halin da nake ciki shikenan sun rabani da aminina kuma farin cikina!”. Wani irin tausayinsa ne ke ratsasu Abba kam kasa daure wa yayi ya sunkuyar da kansa ƙasa hawaye na zuba. Cikin sheshsheƙa Moddibo ya ɗago kansa tare da kallon Ummi idanunsa cike da ruwan hawaye yace. “Shikenan Ummu sunyi mai kisan gillah, sun hanashi shan ruwa, ya mutu da kishi da begenmu, yana ganin muna kiransa amma bashida damar ɗauka, Ummi ashe duk kiran da mukewa J yana kallon kiran mu!”. Sai kuma ya kife kansa akan kwalin hawayen sa na sauka akai yace. “Ummi J yana ganin kiran mu amma bazai iya ɗagawa ba Ummi sun azabtar da J ya mutu da tsananin begenmu da muradin son kasancewa damu Ummi sun cutar da J mutumin da koda ƙwaro baya iya cutarwa bare bil adam shin wani irin zunubi suka aikata!”. Jin ankira assalatu yasa Malam Ahmad sauƙe ajiyar zuciya tare da cewa. “Moddibo kayi haƙuri ku tashi muyi alwala mu tafi masallaci”. Ahankali Moddibo ya ɗago kansa akan kwalin daya jiƙe da hawayensa cikin ransa yace shikenan J ya tafi yabarni bari na har abada shikenan ni kaɗai zan rayu. Hajiya Turai ce ta shigo falon tare da jan Ummi suka tafi ɗakinta Anan sukayi sallah. Dole Gawar M Jameel yanda ya kasance a kakkarye ahaka aka yayyafa masa ruwa madadin wonkan kana aka kaisa makwancinsa na gaskiya. Jana'izar data samu halarta ɗumbin jama'ar domin kafin gari ya waye mutuwar ta zagaye cikin Gembulan da kewayenta har Taraba Yola da dai sauransu. Rayuwa tayiwa duk wani makusancin M Jameel ƙunci da zafi musamman Ummi, Abba, Moddibo, Asma'u, Bashir daga Jiya zuwa yau sunyi wani masifaffen ramewa kallo ɗaya zaka musu kasan cewa suna cikin tsananin ƙuncin rayuwa musamman Moddibo baki daya ya fita cikin hayyacinsa duk ya gigice ya sake zama wani shiru. Misalin ƙarfe biyu na rana bayan andawo daga sallar jana'izar M Jameel Lamiɗo ya koma gidansa kai tsaye falon Mommy ya shiga bakinsa ɗauke da Sallama. Anutse Mommy da Khausar dake zaune suka amsa masa Sallamar. Cike da kulawa Mommy tace. “Sannu da zuwa yinin yau duk baka nan sau biyu ina zuwa sashenka”. Zama yayi akan 3sitter tare da sauƙe ajiyar zuciya kana ya jingina bayansa da jikin kushin ɗin tare da lumshe idanunsa kana yace. “Eh yanzu na dawo daga jana'iza”. Cikin sauri ta kallesa tare da cewa. “Jana'iza kuma?”. Kai ya gyaɗa mata tare da cewa. “Eh”. Gyara zama tayi tare da faɗin. “Janaizar waye!?”. Ajiyar zuciya ya sauƙe tare da dafe kansa kana yace. “Janaizar Jameelu”. Cikin sauri Khausar ta dafe ƙirjinta tare da kallon Lamiɗo kana tace. “Abbah waye”. Kallonta Lamiɗo yayi kana yace. “Malam Jameelu”. Cikin tashin hankali Mommy tace. “Innalillahi wa'inna ilahi rajiu'n Jameelu Yayan Asma'u”. Kai Lamiɗo ya gyaɗa kana yace. “Eh shi ɗin dai Allah ya masa rasuwa”. Cike da kaɗuwa tace. “Innalillahi Ayyah Ummin Asma'u Allahu Akbar duniya yanzu yaron nan kashesa sukayi”. Khausar kuwa tunda ta dafe hannunta aƙirji ta kasa koda ƙokƙwaran motsi ne wani irin bugawa da masifaffen ƙarfi zuciyarta keyi. Atake wani irin kuka mai tsuma zuciya ya kufce mata cikin sheshsheƙan kuka mai cike da tausayi da tashin hankali tace. “Abba Yaya Jameel ya rasu!? Abba kashe Yah Jameel sukayi? Abba me yayi musu da zasu kashesa, suka rabasa da rayuwarsa”. Kai ya gyaɗa mata kana yace. “Eh Khausar sun kashesa kisa mafi ciwo". Sau kuma ya zayyane musu yanda suka samu labarin har suka je wajen da kuma yanda suka samu gawar. Cike da tausayawa Khausar ke jujjuya kai tana cigaba da kuka yayinda numfashinta ke sarƙewa. Kallon Mommy da hawaye ke kwaranya daga idanunta Lamiɗo yayi kana yace. “Tun jiya ne, ai muka samu gasar, ban dai faɗa muku bane, dan kada in hanaku bacci. Yanzu ku shirya anjima idan anyi Sallar La'asar zan kaiku gidan kuyi musu ta'aziyya”. Cikin muryan kuka Mommy ta gyaɗa masa kai cike da rauni tace. “Ayyah Ummin Jameel ta ɗandani mutuwa me raɗaɗi da ƙunan zuciya”. Ta faɗa tana tuno Ramadan domin ko Rasuwar Ramadan bata samu tayi kuka haka ba bayan Lamiɗo ya sake rarrashin sune ya miƙe ya nufi sashen Hajiya Bunayya ya sanar mata. Khausar kuwa Kuka takeyi tamkar zata mace. Bayan anyi sallar La'asar Lamiɗo ya ɗebe su suka tafi gidan Abba. Suna zuwa falon Hajiya Turai suka nufa Cikin gidan da falon cike yake da mutane ƴan ta'aziyya duk wanda yaji rasuwar M Jameel da kuma yanda aka samu gawarsa saiya zubda hawaye tare da la'antar wa anda suka aikata masa haka. Asma'u dake gefen Ummi zaune Idanunta cike da hawaye tana ganin Khausar ta fashe da sabon kuka kana ta miƙa mata hannu cikin sauri Khausar ta kamo hannunta tare da zama gefenta ta. Rungume juna sukay tare da fashewa da wani irin kuka mai tsuma zuciya. Mommy da Hajiya Bunayya kuwa kusa da Ummi suka zauna. Mommy na Kallon Ummi taji wasu sabbin hawaye sun zubo mata cike da tausayawa Mommy tace. “Ummi Sannu”. Sunkuyar da kai Ummi tayi cike da dauriya tace. “Toh ya zamuyi Aysha ya zamuyi da hukuncin Ubangiji. Jameelu ya riga mu gidan gaskiya ya tafi ya barni da gurbin da bansan ya zai cikeminba”. Kai Mommy ta gyaɗa tare da cewa. “Kiyi haƙuri Ummi”. Kasa ƙara sawa tayi sabida kuka yaci ƙarfin ta kawai saita kife kanta gefen Ummi ta shiga rera kuka. Ajiyar zuciyar Ummi ta sauƙe cikin sanyin murya me ɗauke da ƙuna tace. “Kiyi haƙuri Aysha haka Ubangiji ya tsara bamu isa muja da lamarinsa ba addu'ar mu suke buƙata muyi musu addu'a Allah ya gafarta musu”. Cikin sheshsheƙa Mommy tace. “Ameen”. Ahankali Mommy ta juya suka gaisa da Hajiya Turai da Hajiya Karima sannan da ƙannen Abban Jameel Hajiya Maryam da Hajiya Fa'iza suka yi musu ta'aziyya. Khausar dake Rungume da Asma'u cikin Muryan kuka tace. “Asma'u yanzu da gaske Yah Jameel ya rasu shikenan ya tafi ya barmu!”. Kai Asma'u ta gyaɗa tare da cewa. “Da gaske Khausar Yah Jameel ya rasu shikenan gatanmu ya rasu rufin asirin mu ya tafi garkuwan mu ya barmu Inuwarmu wajen fakewar mu ya gushe, bangon da muke jingina muji daɗi ya fadi ƙasa”. Kasa ƙara sawa tayi kawai ta fashe da kuka me tsuma zuciya. Cikin sauri Ummi ta girgiza mata kai Araunane tace. “Kul Asma'u!,Kada ki faɗi haka kada kiyi butulci ga Ubangiji domin shi ya bamu Jameelu kuma shi ya ɗauke mana shi kuma zai jibanci laluranmu muddin mukayi tawakkali”. Innayi dake gefe ta matso kusa da Asma'u da Khausar ta janyosu jikinta tare da ɗaura kansu akan cinyarta cikin Muryan rarrashi tace. “Kuyi haƙuri kuyi masa addu'a”. Ahankali Khausar ta ɗago tare da kallon Innayi kana tace. “Innayi yanzu shikenan Yah Jameel ya tafi ya barmu har abada baza ku sake ganinsa ba!? Bazai sakeyi mana nasihaba, bazai sake neman al'farma a wajenaba ashe Yah Jameel Wasiyya yayi ta barmin a wancar ranar”. Shafa kanta Innayi tayi kana tace. “Khausar kada kiyi kuka muyi masa addu'a shine abinda yake buƙata awajenmu kana mu cika masa dukkan wasiyar daya bar mana”. Kai Khausar ta gyaɗa kana ta cigaba da kuka mai ciwo har Idanunta suka kumbura. Sai Bayan sun idar da Sallar Maghariba kafin Lamiɗo ya ɗebe su suka tafi A wannan daren ranar baki ɗaya haka suka kwana cikin ƙunci zuciya da alhini Moddibo kuwa baya um bare Um-um ko awajen zaman makoki idan akace masa sannu baya magana saidai kallo sai ance Allah ya jikansa kafin yace. “Ameen ya Allah Nagode”. Iya abinda yake iya faɗi kenan. Haka rayuwa tayi musu ƙunci da ɗaci haka aka ɗauki tsawon kwanaki bakwai ana zaman makoki har awannan kwanaki kullum cikin gida da waje a cike yake da masu zuwa ta'aziyya. Washe garin rana ta takwas da safe Moddibo na fita bai nufi ko ina ba sai gidan Ummi bakinsa ɗauke da Sallama yashiga falon zaune ya sameta hannunta riƙe da carbi ta zubawa waje ɗaya ido. Jin Sallamar sane yasa ta ɗago kanta tare da tsira masa Ido agefenta ya zauna. Cikin sanyi tace. “Babana”. Ahankali yace. “Na'am Ummi”. Cike da tausayawa Ummi tace. “Babana kalli yanda ka sake dawowa fa yaushe zaka sawa ranka dangana ne? Kadafa muyi abinda Allah bayaso”. Batare da yace Uffan ba yayi ƙasa da kansa yana jin wani irin zafi azuciyarsa. Jin muryarsa yasa Asma'u dake Bedroom ta fito tare da zama agefensa kana ta gaishesa. Ahankali Moddibo ya juya ya kalli Ummi kana yace. “Ummi yanzu a Duniya babu abinda nake buri daya wuce ingano su waye suka sace J sannan suka yi masa kisan gillah ina so insani. Ummi inaso inyi bincike akai ina so inga lallai a hukunta su kwatankwacin zalinci da suka mana”. Ajiyar zuciya Asma'u ta sauƙe tare da cewa. “Aikuwa Yah Moddibo Khausar tana da dan abinda ta sani. Domin ranan da muka rabu da Yah Jameel na karshe aranan ne ya maida Khausar gida kuma tace mana. Taga wata mota na binsu. Ajiyar zuciya Ummi ta sauƙe kana tace. “Amma Babana Meye amfanin bincike bayan sun kashesa!?”. Cikin sauri yace. “To ai Ummi nan nema yake da amfani tunda suka kashesa dama mun biye musu ne saboda munji tsoron kada su kashesa shiyasa mukabi tsarinsu!”. Girgiza kai Ummi tayi kana tace. “Toh amma dai ni inaganin barin shi yafi A'ala kada kai ɗinma da ka rage mana su cutar mana da kai”. Sam Ummi ta rigada ta saki komai na duniya shiyasa duk yadda yaso ayi mgnar a sake buɗe file din binciken taki. Fahimtarsa bazata yardabane yasa ya nuna mata ya hakura. Kallon Asma'u yayi tare da miƙewa kana yace. “Asma'u zamuyi magana”. Kai ta gyaɗa sannan ya fice. Yau ya kama sati biyu da rasuwar Ramadan wanda yayi daidai da kwanaki sha biyu da jana'izar M Jameel. Acan gidan Lamiɗo kuwa da misalin karfe sha biyu na rana Hajiya Ruƙayya da Mommy da kuma Khausar na zaune afalo suna hira kamar daga sama suka jiyo Sallamar Hajja Nana da faɗin. “Assalamu Alaikum”...! *Kada kyiwa labarin bahagon fahimta. Wasu abubuwa na cikin Labarin gaba ɗaya gaskiyane ya faru da gaske. Ina mai roƙonku da Allah kuyiwa Jameel Addu'o'i Allah ya jiƙamsa da rahama ya kuma toni asirin waɗanda sunka saceshi suka kasheshi kisa mai muni. Ku sashi a addu'o'i ku, domin Wallahi tallahi rasuwar Jameel gsky ne kuma ya faru, da gaske wanda nasan mafi akasarin mazauna Adamawa zasu san labarin rasuwar Jamilu matashi mai Kekkyawan ɗabi'un sun kashewa sun bar mahaifiyarsa da ƙunshin a zuciya, sun sa mahaifinshi a rauni mai ciwo. Yah Allah ka jiƙan Jamilu kayi masa rahama da gafara, ka tausashi zuciyar iyayensa ka ƙara zamewa mahaifiyarsa Gatan* 🤝🏻KADA KUMA KU DAMU ZAKUSHA MAMAKIN YADDA LABARIN ZAI SAKU FARINCI DA SHAUƘI ZAKUSHA MMKIN YADDA LAMARIN ZAI BADA CITTA, KU DAI KU BIYONI KUSHA LABARI, WACCE BATA BIYA TA BIYA. By *GARKUWAR MARUBUTA*